𝑡𝑦𝑝𝑖𝑛𝑔✍️ 𝗠𝗔𝗧𝗔𝗥 𝗗𝗔𝗠𝗨𝗦𝗔 the wife of a tiger🐅🐅🐅 𝙼𝚊𝚕𝚕𝚊𝚔𝚒𝚗 𝙰𝚜𝚖𝚎𝚎𝚝𝚊𝚑 ✍️✍️ 𝙿𝚊𝚒𝚍 𝚋𝚘𝚘𝚔 𝚌𝚊𝚕𝚕 𝚘𝚛 𝚠𝚑𝚊𝚝𝚜𝙰𝚙𝚙 09065443871 *💫💫{{N W A}}💫💫* Book two C̶h̶a̶p̶t̶e̶r̶ 001 ➡️ 002 Ayusher ashe ke mahaukaciya ce bansani ba, ban taɓa sanin ke wawuya bace sai yau, ina kika kai iliminki da kuma hankalinki? shin kinsan abunda kika aikata kuwa..." Ayush tana kuka tace "Uma ki gafarce ni amma bazan iya Auran Yaya Junaid a haka ba..." "yi mun shuru shashasha kawai.." Uma ce ta darara mata tsawa tare da faɗin "ki sani wannan shine dama ɗaya da kike dashi idan kuwa ya suɓuce miki kin rasa har abada, inaso ki sani Junaid ba mutumin banza bane sannan ba manemin mata bane, yana sonki ne yasa har ya fito bainar jama'a ya sanar wa kowa amma ke dakika tashi sai kika watsa masa ƙasa a ido, duk abunda zakiyi ki rinƙa hango gaba domin baya ya rigada ya wuce, burina bai wuce ki Auri Junaid ba saboda zaifi samun nutsuwa a wajenki kuma haka mahaifiyarsa a duniya bata da burin daya wuce Junaid ya Aure ki, inaso ki sani cewa wannan baikon da aka haɗa mahaifiyar Junaid ce ta yanke wannan hukunci, kuma tin ba yau ba take son haɗa soyayyarku, Ayush ki mata adalci mana ko dan ita ki Auri Junaid mana, tana matuƙar ƙaunarki duk da har yanzu basu san asalin ki ba..." miƙe wa Ayush tayi tana kuka tace "yanzu Uma kin goyi bayan na Auri Yaya Junaid?.." ajiyar zuciya Uma tayi sannan tace "ba shawara nake baki ba, umarni nake baki, idan kuwa kika tsallake ki sani babu ni babu ke kuma bazaki sake ganina ba har abada...." Ayush kuka ne ya kuɓuce mata sosai jin abunda Umanta tace, suna cikin wannan halin suka jiyo takun takalmi an nufo ɗakin, da sauri Uma ta shige cikin toilet, ita kuma Ayush zama tayi a bakin gado ga hawaye caɓa-caɓa a fuska, turo ƙofar ɗakin akayi, rai a ɓace Angel tayo kan Ayush tana faɗin "Ayush wai mekika aikata haka? haba dan Allah yanzu kin kyauta kenam, nasan Ogah Junaid yana matuƙar ƙaunar amma kika rufe ido kika ci masa mutunci a cikin mutane, wallahi da abunda kika masa gwara ki zabga masa mari kiyi tafowarki, ya amshi soyayyarki da ƙwarin gwiwa amma kee...." ta ƙarasa maganar tana sharar hawaye, miƙewa Angel tayi tareda faɗin "sakamakon abunda kika aikata ya jawo ciwon heart ɗin mommy ya tashi yanzu haka sun nufi hospital da ita, shi kuma Junaid ganin yanda mommy take amar da jini yasa shima ya faɗi sumamme saboda tin baya likita ya sanar masa cewa idan zuciyar mommy ta sake bugawa zata iya rasa rayuwarta, ki duba ki gani duk ata sanadiyarki ki ruguza farin cikin dubban al'umma, masu Allah wadar da halinki su sukafi yawa, banji daɗi ba sam...." tana kaiwa ƙarshe tayi ficewar ta.. Ayush ba abunda take sai kuka fuskarta yayi jawur, Uma ce ta fito daga toilet itama tana kuka tace "kin kyauta Ayush aikinki na kyau, amma inaso ki sani indai mommy ta mutu zaman cikin gidan nan ya ƙare miki, kuma kinyi rashin babban ɗan uwanki, jininki kuma masoyinki, ki sani duk wanda zaki aura bazai kai Junaid ba domin shi ɗin farin cikin rayuwarki ne..." Ayush ta buɗe baki zatayi magana Uma tayi saurin ɗaga mata hannu tareda faɗin "sai anjuma.." ficewa tayi itama daga ɗakin, tana fita ta murɗa zoben hannunta lokaci ƙanƙani ta ɓace ɓat... bayan fitar Uma daga cikin ɗakin Ayush hannu ta ɗora a kayi ta rusa wani irin gigitaccen ihu! kuka take sosai na fitar hankali, Mommy har zuwa yanzu bata daina amar da jini ba, tana kwance a gadon asibiti likitoci sun fi biyar akanta, wasu suna danna mata ƙirji sakamakon harbawa da yake da ƙarfin gaske, cikin gaggawa aka ɗaura mata ledar jini, idonta sun fiffito waje tana shaƙar numfashi daƙer, dasauri aka sanya mata oxygen still ana daddanna mata ƙirjinta ta saitin zuciya.. and other room Junaid ne yake ƙwance shima an ɗaura masa ledar ruwa sakamakon zafin da jikinsa ya ɗau duk ruwan jikinsa ya yi low, a wannan lokacin shima bai samu farfaɗowa ba, ata waje kuma Rumana ce da Aditi suke zaune zaman jiran farfaɗowarsu, Doctor Hasheem shima yana daga cikin likitocin da suke duba mommy, abokatan Junaid duk suma suna nan, Angel ce ta shugo asibitin da saurin ta hawaye duk ya wanke mata fuska, guri ta samu itama ta zauna a kujerar da su Aditi suke a zaune, babu wanda aka bari a gida sai iya Ayush... tana kwance a saman gadonta sai faman rera kuka take, a ranta bata so hakan ta faru ba, inda tasan Mommy ce ta haɗa da batayi gangancin lalata shirin ba, ji tayi an dafa bayanta, da sauri Ayush ta zabura ta tashi zaune ido duk yayi dishi dishin jaa tana kallon Laylah wacce take zaune a bakin gadonta, murmushi Laylah tayi sannan tace "kukan mai kike yi? saboda kin faɗi abunda ke ranki shine kike ƙoƙarin kashe kanki? ni banga laifinki ba don kin fito fili kin sanar cewa bakya son abunda ake shirin ƙaƙuma miki" ajiyar zuciya Laylah tayi sannan ta kuma cewa "ni yanzu dai ba wannan ne ya kawoni ba, nazo ne akan na baki haƙuri akan abunda ya faru abaya, nasan nayi kuskure kuma nayi nadamar yin haka, please Aunty Ayush kiyi haƙuri dan Allah..." Ayush share hawayen fuskarta tayi daƙer take motsa baki tace "ba komai ya wuce.." fuska duk ya kumbura! Laylah tace "are you sure my Aunty?" Ayush ɗaga mata kai kawai tayi saboda bata son magana a halin yanzu.. Laylah tace "ok thanks, kinsha kuka sosai nasan kanki dole zaiyi ciwo, ki kwantar da hankalinki su mommy zasu dawo gida cikin kwanciyar hankali, yanzu dai ga wannan maganin ciwon kai ne kisha sai ki samu yin bacci ko?..." Laylah buɗe jakar ta tayi ta ɗauko wani magani ƙananu ta ɓare ta bawa Ayush tareda buɗe murfin gorar ruwa dake hannunta, Ayush karɓa tayi tana faɗin "nagode.." Laylah tace "ba komai nima ina fama da ciwon kai ne shiyasa nake yawo da maganin" ta ƙarasa maganar tana kallon Ayush ta wutsiryar ido tareda cije leɓɓen bakinta.. bayan Ayush tasha maganin gaba ɗayansu shuru sukayi ba wanda yace wa wani ƙala acikinsu, after 5 minute dishi-dishi Ayush ta fara gani, idonta yana shirin rufuwa, gani tayi kwakwalwarta ta fara juyawa, nan take ta nemi hankalinta ta rasa, miƙewa tayi tsaye tana tangal-tangal murya na rawa tace "meyake faruwa dani ne, gajimare nake gani, ga can wasu da dokuna suna taho wa..." ganin Ayush yanzu babu wani hankali a jikinta yasa Laylah ta tintsire da dariya tana tafa hannayenta biyu tareda faɗin "yaro man kaza, yaro bai san wuta ba saiya taka, Ayush kenam ni ba kanwar lasar ki bace, duk wanda ya raɓi jikin Junaid sai yanda ƙarfina ya ƙare wallahi, nasan wannan abunda ya faru yanzu bashi zaisa Junaid ya rabu dake ba, koda ace shi baya yinki nasan mommy saitayi kinibibin haɗa ku kuma duk da nasan a yanzun ma ita take shirin haɗa auren nan, amma yanzu zan kawo ƙarshen komai, zan dasa tsanarki a cikin zuciyar Ogah Junaid wanda ko kallonki bazai so ya yi ba, zansa ya rinƙa ƙyamarki..." tana kaiwa ƙarshe ta ƙwashe da dariya, ita kuma Ayush zama tayi a kusa da Laylah tana ta faman shafa ta, tareda rungumota tana faɗin "inasonka sosai da sosai bazan iya rabuwa da kai ba masoyi, dan Allah ka bani kulawarka a gareni.." tana maganar kamar wata ƴar maye.. mirmushin gefen baki Laylah tayi sannan ta ɗauki wayarta ta kara a kunne bayan tayi dialing call, "Hello sauro ka shugo yanzu ina jiranka, ɗakin dana kwatanta maka nan zaka shugo, kayi sauri kaga ba kowa a gidan.." tana kaiwa ƙarshe ta katse ƙiran, ga kuma yanda Ayush ta rungumeta sosai a jikinta... Laylah wani magani ta bawa Ayush na fitar da mutum daga hayyacinsa sannan ya dasa masa mungun sha'awa, ta ƙira wani ɗan daba ne domin yazo yayi mata aiki akan Ayush.. ba jumawa saiga mutumin nan ya shugo cikin ɗakin Ayush yana ɗaure da fuska irin nan ba mutunci, rufe ƙofar yayi sannan ya danna sakata tareda cire kayan jikinsa ya zauna daga shi sai short nicket iya cinyarsa wato pant na maza.. ƙaƙƙarfan namiji ne irin zabgegen mazan nan, yana zuwa ya haura saman gadon tare da janyo Ayush ya cire mata kayan jikinta ya barta daga ita sai braziya da kuma gajeran wando baije mata gwiwa bama, ita kuma sai shafa jikinsa take duk gargasa yayi curɓu-curɓu ba kyan gani, amma da haka Ayush take rungumarsa tare da shafa shi tana ta surutai "ina sonka, bazan rabu da kai ba, dan Allah karka ƙyaleni, inason kasancewa tare da kaii.." shima shafa ta yake ta ko ina, yana cusa hannunsa cikin breziyar ta tareda kissing ɗinta akan ƙirjinta, Laylah kuwa tana tsaye ba abunda take sai video, tana musu ɗauka na gaske gashi sun fito sosai, har muryar Ayush ta fito yanda take ta surutai duk a rashin sani, Laylah ganin mutumin yana shirin cire sauran kayan Ayush da kuma nashi ta danna stop sannan tace "kai sauro dakata nifa bance kayi mata komai ba, romance kawai nace kayi da ita.." cikin ƙatuwar murya yace "na bar miki kuɗin da zaki bani, kawai ki barni nayi amfani da ita, wannan kyakykyawar budurwa zankaɗeɗiya wazai gani ya ƙyale...." Laylah tace "kaga sauro ba haka mukayi dakai ba saboda haka kayi yanda nace, kuɗinka zan baka amma kada ka kuskura kayi mata wani abu, ina tausayin ƴan uwana mata saboda haka bazanso a cutar da rayuwarta ba, ka hau kanta kawai kana kissing ɗinta, kaga ba lokaci.." yanda tace kuwa haka yayi amma ba'a son ransa ba, ta cigaba da musu video, shi kuwa kwantar da ita yayi ya hau kanta yana sumbatarta ta ko ina, itama Ayush tana ƙanƙame dashi hannayenta yana zagaye ta bayansa, bakinta kuwa ya kasa rufuwa sai sambatu take tana faɗan maganganun batsa ta yanda zaiyi amfani da ita..." daga ƙarshe Laylah ta bashi umarnin ya sauƙa haka, tayi saved video tana cije leɓɓenta, saka kayansa yayi sannan yace "ƴanmata ni zan tafi saina ji alart, ɗaga masa kai kawai tayi sannan tace "yanzu ma kuwa.." yana tafiya tayi masa transfer 50,000, Ayush kuwa nan danan wani irin mungun bacci ya ɗauketa, dariya Laylah tayi tace "wooo ni Laylah Amaryar Ogah Junaid, Ayush kenam daga yau soyayyarki bazata ƙara zama a cikin zuciyar Ogah Junaid ba, nasan dai bayan kin farfaɗo bazaki tuna abunda ya faru ba, sai dai ki ganki acikin wannan yanayinda kike ciki, na barki lafiya..." Laylah ce itama tayi ficewar ta a ɗakin, cike da farin ciki ta bar gidan gaba ɗaya.... Ayush bata farfaɗo ba sai ana ƙiran sallar mangarib ta tashi jikinta yana mata ciwo, ga ta tashi da ciwon kai tana lumshe manya-manyan eyes ɗinta waɗanda suka shanye kamar wacce tayi maye, kallon kanta tayi a zabure ta tashi tana faɗin "subhanallahi ya na ganni a haka?.." kallon yanda kayanta suke a saman gado tayi tana mamakin yanda akayi ta cire kayan ta, can bayan ta zurfafa tunani tace "waɗannan kayan masu uban zafi daman taya zan iya kwanciya dasu, mantawa kawai nayi ina buƙatar shan iska.." ta sauƙa daga saman gadon taje gaban madubi ta tsaya tana kallon kanta, ita bata kawo komai a ranta ba saima tuno da Mommy datayi a asibiti tareda Junaid, hawaye ne suka fara mata go slow asaman fuskar ta, taga bisani ta goge hawayen ta shige cikin toilet tayi wanka da ruwan zafi sakamakon ciwon da jikinta ke mata, ta fito ta shirya tsab ta zura ƙatoton hijab har ƙasi tayi sallah kafin ta tashi ta fice daga cikin ɗakin, tunani tayi gwara kawai taje asibitin taga meyake faruwa duk da tasan zata fuskanci wulaƙanci ga kuma yunwar da take ji amma bata buƙatar cin komai a halin yanzu... tana fito wa harabar gidan kai tsaye hanyar da zai sadata da gate ta nufa, sai da tayi tafiya mai ɗan nisa kafin ta iso bakin gate hijab ɗinta na jan ƙasa, Baba maigadi ne ya fito yana faɗin "ke! ke ina zakije kina ganin duhu ya gabato?.." tace "zanje dubowa mommy a asibiti.." Baba maigadi yace "amma yarinya idan dare yayi ba'a samun abun hawa a wannan yanki fa.." tace "karka damu zanje bakin hanya.." ya ce "la la laaa da ƙafarki? amma yayi miki nisa daga nan ai.." Ganin zai ɓata mata lokaci yasa tace "Baba buɗe mun gate ɗin nan zan tafi a haka, Yaya Junaid yana can yana jirana shi yace naje ni yanzu" Baba maigadi yace "ayyo ai saiki mun bayani tin farko, zo ki wuce.." ya buɗe mata ta fice, tafiya take da sauri- sauri saboda unguwar shuru ba kowa sai hasken nepa ta ko ina amma gidaje a ƙarƙame da gate, unguwar GRA kenam, da haka ta isa bakin hanya a tsorace, tana zuwa ta tari mai adaideta sahu ta hau sai asibitin Doctor Fateema.. suna isowa da sauri Ayush ta sauƙa zata shige cikin hospital saboda secuirity bakin gate sun hana shiga da abun ƙarfe ciki saidai idan ma'aikatan asibitin ne, mai keke napep ne ya kwalla mata ƙira yana faɗin "Hajiya kin manta baki ban kuɗina ba.." jin haka yasa Ayush tsayawa ta juyo tace "nawa ne kuɗin?" yace "ɗari biyar ne, kinsan da daddare ba'a ɗauka sosai..." Ayush dai tsayawa tayi tana kallon mutumin, ga ba sisi a hannunta, sai cewa tayi "malam dan Allah kayi hakuri banida kuɗi wallahi...." kafin ta rufe baki ya katse ta da cewa "a'ahh wallahi ba wannan maganar kawai dai ki ban kuɗina yawwa.." Ayush cikin sassanyar murya tace "toh shikenam jirani zan kawo maka kuɗin ka yanzu.." yace "toh ina jiranki yanzu" ta shige ciki tana gudu ita burinta taga majinyatan a wani hali suke. tana shiga can cikin compound na asibitin ta tarar da Angel tana tsaye ta jingina da jikin gini kai a sama, Aditi da Rumana kuma suna a zaune, har Aditi ta fara gyangyaɗi domin so suke suga farfaɗowar Junaid kafin su wuce gida, Mommy kuwa sun san wannan sai anyi da gaske tukun.. jin shugowar Ayush yasa suka juyo suna kallonta, Rumana kam kallo ɗaya tayi mata taja dogon tsuka sannan ta kawar da kanta gefe, itama Aditi tana kallo Ayush ta maida kanta tana cigaba da baccinta, Angel kuwa kanta a sama tana kallon ceilling ko kallon Ayush batayi ba sakamakon dogon tunani data zurfafa bata ma san Ayush ta shugo ba... itama Ayush tsayawa tayi bata ce musu ƙala ba ta samu ɗaya daga cikin kujerun wajen ta zauna, ƙirjinta kuwa na bugun uku-uku a tsorace take gaba ɗaya, tunanin kalar wulaƙancin da Junaid zaiyi mata take yi, ta saddaƙar ƙarshen barinta gidan kenam, bazai cigaba da zama da ita ba, itama zufafa tunaninta tayi suna cikin wannan halin suka ji ance "hajiya ya zaki shanya ni a waje kince zaki karɓo mun kuɗina..." Ayush firgitt tayi har ta tsorita da jin maganar mutumin mai keke napep, kamar zata yi kuka tace "haba bawan Allah ba'a temako ne?.." yace "dakata hajia nifa ba temako na fito yiba yauwa neman kuɗina na fito yi, ina zaune ba mai temaka mun nima..." Aditi da Rumana kam ko kallon wajen basuyi ba saboda ba jin abunda suke faɗa sukeyi ba, kwata-kwata basu iya hausa ba, Angel ce kawai ta iya hausa sosai saboda ta zauna a cikin hausawa, ta kalli yanda suke tace "meyake faruwa ne?" kafin Ayush ta buɗe baki har mutumin ya kora mata jawabai, Angel bata ce musu komai haka ta buɗe handbag ɗinta ta ciro 1k ta bawa mutumin tace "gashi nan kaje kawai..." mai napep washe baki yayi yana godiya ya kalli Ayush yace "hajiya saida safe koh..." ko kula shi batayi, ta kalli Angel tace "nagode..." bata kai ƙarshe ba suka jiyo likita yana cewa "zaku iya shugo wa Ogah Junaid ya farfaɗo tin ɗazu ya samu hutu ne yasa ba'a ƙira ku ba.." da sauri suka miƙe cikin room ɗin da Junaid yake ciki, Ayush kawai aka bari zaune a gurin ta kasa tashi ma, gabanta sai yanke wa yake, bayan sun shiga Aditi da Rumana ne suka zauna a bakin gadon da yake, Angel kuma tana tsaye sai murmushi take ta zubawa, tana farin cikin tashin Junaid, shima yana zaune har an cire masa ledar ruwan da aka ɗaura masa, kwata-kwata ba annuri a fuskarsa, su kuma sai masa sannu suke suna gaishe shi da jiki, baya iya ce musu komai sai kawai ɗaga musu kai yake, ya kalli yanda Angel take a tsaye yace "ina mamana?.." Angel tace "tana other room ta samu yin bacci ne, amma da zarar ta tashi za'a sanar maka.." tayi masa wannan dabarar ne saboda kar yace zaije ya dubata, gashi ba'a barin kowa ya shiga sai likitoci.. kaɗa kansa kawai yayi, gaba ɗaya jikinsa yayi sanyi, yana zaune ya kasa cewa komai, suma duk cikinsu ba wacce ta ƙara yin magana, sake ɗagowa yayi ya kalli Angel yace "ke bakya gajiya da tsayuwa ne? ko sojoji basa gajiya ne.." murmushi tayi tana kallonsa cike da mamakin yanda ya canza lokaci guda, tace "ina zuwa..." ta juya ta fice daga cikin ɗakin.. shi kuwa binta yayi da kallo har ta ƙule masa kafin ya kawar da kansa ya maida kallonsa kan su Rumana da Aditi waɗanda suke zaune daf dashi a bakin gadon.. bayan wasu seconni sai ga Angel ta shugo tana riƙe da hannun Ayush, har suka iso gaban gadon da Junaid yake a zaune, tin shugowarsu Junaid ya kafa idonsa akan Ayush kamar zaiyi kuka haka yake kallonta, itama Ayush fuska yayi jaga-jaga da hawaye ga idonta ya kumbura sosai tsabar kuka haka suka tsaya suna kallon juna ido cikin ido. Aditi da Rumana kamar zasu haɗiyi ransu tsabar takaici sai suka tsaya suna kallonsu, Angel kuma ba abunda take sai murmushi, sarkin murmushi kenam bata fushi...... 𝑡𝑦𝑝𝑖𝑛𝑔✍️ 𝗠𝗔𝗧𝗔𝗥 𝗗𝗔𝗠𝗨𝗦𝗔 the wife of a tiger🐅🐅🐅 𝙼𝚊𝚕𝚕𝚊𝚔𝚒𝚗 𝙰𝚜𝚖𝚎𝚎𝚝𝚊𝚑 ✍️ 𝙿𝚊𝚒𝚍 𝚋𝚘𝚘𝚔 𝚌𝚊𝚕𝚕 𝚘𝚛 𝚠𝚑𝚊𝚝𝚜𝙰𝚙𝚙 09065443871 *💫💫{{N W A}}💫💫* Book two C̶h̶a̶p̶t̶e̶r̶ 003 ➡️ 004 Kawar da kansa gefe Junaid yayi daga kallon Ayush, Angel ce tayi wa su Aditi magana ta turanci tace "ku taso to suna son yin magana.." Rumana ce ta juyo tana watsawa Angel harara da waɗannan blue eyes ɗinta, itama Aditi ƙara curɓune fuska tayi tana faɗin "ba yanda zanje ni, ayi komai a gaban mu" ajiyar zuciya Angel tayi tana kallon Junaid ko zaiyi musu magana, amma ko juyowa baiyi ba yana kallon gefensa, Angel ce tayi wa Ayush raɗa a kunne tace "ki zagaya ta gefen da yake kallo.." Ayush kallon Angel tayi da sauri tana girgiza kai tace "ina tsoro kar ya mareni.." turata Angel tayi tana faɗin "jeki ba abunda zaiyi miki" gaba ɗaya jikin Ayush a mace yake batada wani ƙwari haka take jan sawayenta daƙer kamar mai tambayar ƙasi, Rumana ƙara juyowa tayi ta harari Angel tareda faɗin "munafuka kawai kinason haɗa abunda bazaiyu ba" murmushi kawai Angel tayi bata tanka mata ba.. Ayush tana zuwa gaban Junaid yanda yake kallo ta zauna a bakin gado daf dashi, zuciyarta na bugawa da ƙarfin gaske da haka tana ɗarɗar ta ɗago da hannayenta da suke ta kakkarwa ta kamo hannun Junaid duk biyun ta riƙe sosai a cikin nata tana fuskartarsa ga hawayen da yake ta zuba asaman fuskarta, baki na kakkarwa cikin sassanyar murya tace "Yayana! Yayana!! Yayana kayi hakuri, nayi kuskure babba dan Allah ka gafarce ni...." kukan da take ƙunshe dashi ne ya kuɓuto mata, kuka take rerawa sosai kai a sunkuye tana kallon ƙasi domin ko ido ta gagara haɗawa dashi! ɗakin yayi tsit sai sautin kukan Ayush kake ji, duk ta wanke masa hannayensa da take riƙe dasu da hawaye, zamar da hannunsa yayi daga cikin nata ya riƙo haɓarta sannan ya ɗago da kanta suna kallon juna, yace "bakiyi kuskure ba Yushert, dan kin fito kin faɗi abunda yake ranki ai ba laifi bane, duk laifi nane da ban sanar miki maganar baikon ba! da hakan bata faru ba, inasonki ne yasa na amince da Aurenki amma tinda bani ne a zuciyarki ba ai baza ayi miki dole ba, domin nima mai iya Aurar da ke ne ga duk wanda kike so, itama mommy abun tasa a ranta ne yasa har ciwonta ya tashi, Yushert! kamar yanda bakya sona insha Allahu nima zanyi ƙoƙarin cire sonki daga cikin zuciyata, karki damu ki kwantar da hankalinki.." ya ƙarasa maganar yana ɗaga mata kai... wani sabon kukan ne ya sake kuɓuto mata, wani irin raɗaɗi take ji a cikin zuciyarta tana saƙe-saƙe a ranta "wai ma taya zance bana son Yaya Junaid? bayan shine mutumi na farko dana taɓa so a rayuwata kuma nake da burin Aurensa wayyo kaico nahh.." rera kuka take sosai ta ɗora hannayenta biyu a kanta, ido a rufe sai fama kuka take ga fuskarta nan yayi jawurr idanuwanta sun kukkumbura ga sunyi jaa, gumine yake mata go slow daga cikin sumar kanta zuwa fuskarta ga ya haɗu da hawaye sai fuskar tayi jaɓa-jaɓa kamar wacce ta feshe fuskar da ruwa, Junaid kafa mata eyes yayi yana ganin yanda take ta ɓare masa ɗan ƙaramin bakinta tana kuka, shima idonsa kamar mai jin bacci yayi lufu-lufu ya kalli yanda Angel take a tsaye yayi mata alama da kansa akan tazo ta ɗauki Ayush suyi waje saboda baya son jin kukan Ayush hakan yana taɓa masa zuciya, bazai iya juran ganinta a cikin wannan yanayin ba, Angel zuwa tayi ta riƙo hannun Ayush tana faɗin "taso mu tafi.." murya ciki-ciki Junaid yace "kuje gida ki rarrashe ta" ya kalli yanda su Rumana suke a zaune ko waccen su fuska a hargutse babu wani annuri a tattare da fuskarsu yace musu "kuma ku tashi kuje gida ina buƙatar hutawa, zan zauna da mommy..." Aditi ce tace "to ku sai yaushe ku dawo?" in short answer yace "till tomorrow..." su kuma Angel har ta fice da Ayush... Rumana ce ta tashi sannan ta rungumo Junaid tareda kissing ɗinsa a gefen fuskarsa, tace "gud night my Romeo..." murmushi kawai yayi tare da ɗaga mata kai, itama Aditi miƙewa tayi har sai data hau saman gadon tukun ta rungume shi sosai kafin ta ɗago ta naushe shi a ciki, ƙara ya ɗanyi kaɗan tareda dafe cikinsa ya ɗago yana kallonta yace "you are crazy Aditi, stupid girl..." kallonsa take up and down tana fari da ɗan ƙananun eyes ɗinta tace "na raga maka ne saboda kana kan gadon asibiti amma ba dan haka ba sai munyi dambe, laifi biyu ka aikata mun na farko dukan daka mun, na biyu kuma shine babban laifin daka aikata wato kana son ka yaudareni ko? kana shirin yin engagement da wata ƙaramar yarinya gud sai mun haɗe a gida..." murmushi yayi sannan yace "mu haɗe ki ci ƙaniyarki ba.." murmushi tasau masa kafin tace "good night my Hero" baice mata komai ba haka itama ta fice, suna fita ya miƙe tsaye tareda kallon agogon da yake manne a ɗakin ƙarfe 9 na dare yanzu, yazo zai fita saiga Doctor Hasheem ya shugo yana cewa "ha'a Ogah Junaid ina zuwa haka?..." amsa ya bashi yana faɗin "I what to see my mom.." dariya Doctor yayi tana faɗin "haba Oga Junaid sai kace wani ƙaramin yaro, mommy tana bacci bata farka ba, ka kwantar da hankalinka zuwa gobe zaka ganta.." Junaid rai a ɓace yace "har sai gobe? duk banga halin da mahaifiyata take ciki ba? impossible.." yana kaiwa karshen maganarsa ya ratsa ta gefen Doctor Hasheem yayi ficewarsa.. shi kuwa Doctor Hasheem kallonsa kawai yayi ya girgiza kansa yana murmushi da jaka a hannunsa daman yana shirin tafiya gida ne, Motarsa yaje ya shiga da gudun gaske yabar asibitin.. ☆☆☆☆☆☆ "Lailah kinga banaso ki bari meye haka?..." Maimoon ce take faɗar haka tareda tutture Lailah gefe, Lailah tace "haba Besty na ya zaki mun haka? yanzu rabon damu ji daɗin junan mu tin yaushe? wallahi ina fama da munguwar sha'awarki ki temake ni mana my Besty..." Maimoon cikin ɗaga murya take cewa "Lailah daga ke har Yayanki bana jinku a raina, tinda har zaki iya goyon bayansa akan abunda yamun a haɗa baki dake kici amanar mahaifiyata kika ce na ɓata alhalin kuna ƙunshe dani a cikin wannan akurkin ɗakin nakun, ni yanzu ba abunda zaki cemun Lailah.." ajiyar zuciya Lailah tayi sannan tace "kinga Maimoon yanzu ba'a cikin hayyacina nake ba, burina yanzu in fitar da abunda ke damuna a marata.." ta ƙarasa maganar tareda janyo Maimoon ta rungumeta sosai tana ƙoƙarin haɗe musu baki, ita kuwa Maimoon kaucewa take tana faɗin "ni ki barni yanzu bana jin hakan a raina, Allah ya yaye mun..." Lailah ce ta hau saman Maimoon har taci nasarar haɗe musu baki guri ɗaya, socking take kamar kamar zata cinye bakin Maimoon, hannunta ɗaya akan breast ɗinta sai faman matsasu take, acikin Maimoon tana tutture ta har jikinta ya mutu ko motsi bata iya yi, hakan ya bawa Lailah damar cire mata kayan jikinta, hatta breziya saida ta cire ta kama nipple ɗin Maimoon da baki tana jansa cikin salo da ƙwarewa, numfashi take fitarwa sama-sama tana nishi itama Maimoon harta fita hayyacinta, Lailah hannu ta fara tusawa acikin pant ɗin maimoon tana shasshafawa a hankali sakamakon bata gama warke wa ba, sai da ta tabbatar da tayi realized kafin ta sauƙa daga kan Maimoon, sai yanzu taji jikinta yayi wasar..." ɗan tsuka taja kafin tace "duk Ayush ce wallahi ta tayar mun da feeling tana wani shafani wai masoyi, zata ga unreachable ai indai ni ne Lailah.." duk abunda Lailah take faɗa maimoon tana jinta still tana kwance ta gagara tashi, ta ɗora hannunta saman fuskarta tana kallon sama, gaba ɗaya wani irin ƙololuwar baƙin ciki take ji a ranta, gashi Lailah tasa tayi abunda batayi niyar yinsa ba.." tashi Lailah tayi tana shirin fita daga ɗakin tace "Besty zanje nayi wanka sai nayi cooking nasan kina jin yunwa ko?..." haka Lailah ta gama surutanta ta fice, ita kuma Maimoon ko kalonta batayi ba balle ta sa ran zata kulata.. tana fita saiga Doctor Hasheem shima ya nufo ɗakin, ganinsa yasa ƙirjin Lailah bugawa ta zaro ido waje tace "Bros yanzu ka dawo ne?..." yace "eh mana daman bakiyi bacci bane?" tana ƙinƙina tace "am am eh eh wallahi nazo taya Aunty maimoon hira ne, zaman kaɗaici ba daɗi.." jinjina kai kawai yayi sannan yace "ok ya kamata kije kiyi bacci yanzu, idan kinje falo ki buɗe frig zakiga ledar fruit saiki ci kafin ki kwanta, gana maimoon itama yanzu zan sakata taci natan..." Lailah tace "toh my bros mun gode" yace "to bani key ɗin ɗakin nan" ta miƙa masa sannan tabar wajen da sauri, shi kuwa ya shige ɗakin.." yana shiga ya tarar da maimoon kwance, riga a zame tana kallon saman ceilling rigarta ne kawai a ɗan ɗosane saman breast ɗinta, wanda ana zamar dashi shikenam, ga kuma breziya a gefe, binta yake da kallo cike da mamaki yazo daf da ita sannan ya zauna a bakin katifa yace "maimoon ya haka? meyasa kika cire rigar takin ga kuma rigar breast a gefe kuma ai ba zafi kike ji ba tinda ga iskar fanka ta ko ina.." tana daga kwance ko motsawa batayi ba tace "ka tambayi ƙanwarka mana.." saida gabansa ya faɗi yaji wani rass yace "ƙanwata kuma? bangane mai kike nufi ba." shuru tayi masa batace komai ba, ya ƙarishi maganarsa amma kota kulashi, ajiyar zuciya yayi sannan yace "ok tinda kin ƙi yin magana tashi kici abinci nasan kina jin yunwa ko?.." mirginawa tayi tana kallon bayanta tace "bana buƙata" murmushi yayi sannan yace ki temaka mun ki tashi kici.." miƙewa tayi ta zauna a fusace tace "kai malam taya kake son na rinƙa biye maka ne, nace banaso shin ana dole ne, idan nace banason abu to bana sonsa, kuma gwara yunwa ta kasheni indai ni zanci abun hannunka..." tana kaiwa ƙarshe ta tashi tana ɗingishi zata nufi toilet ga riga a hannu ta tare nonuwanta dashi, Doctor Hasheem riƙo hannunta yayi ya jawota jikinsa yana faɗin "meyasa kika raina ni ne maimoon? meyasa har yanzu baki yadda da ƙaddara ba, wannan abunda ya shiga tsakanin mu tsautsayi ne.." katseshi tayi da cewa "ni ka sakeni meyasa kuke mun hakane kai da Lailah kun mayarni tamkar jakar ku, na tsaneku wallahi" gaba ɗaya ya kasa gane ina ta dosa sai cewa yayi "please maimoon ki nutsu mana, abinci...." idonsa ne ya sauƙa akan manya-manyan nonuwanta masu sheƙi dake farar fata ce, rigar data rufesu dashi ne ya zame, wani irin haɗiyar yawu yayi tinin har ya shiga taitayinsa, a hankali ya janyo rigar ya rufe mata su yakai idonsa saman fuskarta yaga itama shiɗin take kallo, ɗan yatsarsa yakai saitin bakinta yana faɗin "kiyi shuru ki zauna ki ci kayan fruit ɗinki.." zaunar da ita yayi sannan ya buɗe ledar ya ɗauko ayaba ya ɓare sannan ya fara feeding ɗinta, a bata son haka ta haƙura take ci... ☆☆☆☆☆☆ Junaid bayan ya tambayi ɗakin da mommy take aka nuna masa ya shiga, zama yayi a bakin gado ya zuba mata ido har ƙwalla ta soma cicciko masa, ya kamo hannunta ya rinƙe, ita kuma tana kwance bata farfaɗoba anyi covery baki da hancinta da oxygen, jinin da aka ɗaura mata ne yake ɗigowa da kaɗan kaɗan, yanzu ledar jini huɗu ta sha.. ☆☆☆☆☆ bayan isar su Ayush gida, Rumana ce ta nemi guri ta zauna ta ɗora ƙafa ɗaya akan ɗaya tana kallon plasman dake film ɗin turawa ake showing.. Aditi kuma wuce room ɗinta tayi tana faɗin "yunwa nake ji a nema mun abunda zanci kafin na fito.." Angel ce ta kalli Ayush tace "to ki cire wannan ƙaton hijab ɗinki mana..." tasa hannu ta cire mata shi, itama Ayush ɗin zama tayi tana kallon, Angel kuma ta nufi kitchen zata dubo musu abun taɓawa, cikin sa'a kuwa ta samu ferfesun chicken a cikin ƙatuwar kula da zafinsa, haka ta ɗauki kular gaba ɗaya ta fita dashi falo da plate guda huɗu, tazo ta zuzzuba musu ta ɗauko lemuka masu sanyi a cikin frig Aditi fitowarta kenam ta tarar an shirya komai na abinci, ta zauna tareda janyo plate da lemon a gabanta, suma sauran ɗauka sukayi suna ci ba wanda ya kula kowa a cikinsu, Ayush daƙer take cin domin bata jin cin komai saboda damuwar da ya sakota a gaba, kafin ɗan seconni Aditi ta gama da nata tace "ni saboda an raina mun wayo sai a sako mun chicken ɗan kaɗan kenam.." Angel ta kalle ta tace "yanda nasa miki haka na sawa kowa, acici mala'ikun tauna" a fusace Aditi ta tashi ta buɗe kular ta cika plate ɗinta dashi kafin ta zauna nan ma ta cinye tass, sauran kuma duk ba wacce ta iya cinye nata, bayan sun kammala tsab Rumana ta cigaba da kallonta domin bata son draman ya wuce ta, Aditi ce itama ta zauna saman sofa tareda ɗaukar remote tana faɗin "mai zamu kalla a masu korayen idanuwa.." ta canza film ɗin da Rumana take kalla, ta sauya da film ɗin china. Angel tazo gaban Rumana ɗaukar sauran chicken dake cikin kular! Rumana ta wani canki kular da ƙafarta sai ferfesun ya kwacaɓe a jikin Angel duk ya ɓata mata abaya gashi mai ruwan milk ne, ita a dole ta fusata ne yasa ta canki kular ta miƙe da sauri tayo kan Aditi zata karɓe remote ɗin, tana faɗin "ba abunda zamu kalla a masu ƙananun idanuwa..." suka kaure da kokuwa suna dukan juna a tsakanin Aditi da Rumana, sai ga Angel itama ta miƙe a fusace tayo gurinsu, ɗago kafaɗar Rumana tayi ta zazzabga mata mari a fuska har sau huɗu tace "ke makahuwa ce kina kallo kin mun wanka da miya amma ko a jikinki?..." Rumana hannu takai itama zata mari Angel tayi saurin riƙe mata hannu tareda ƙara zabga mata mari, daiden lokacin Aditi ta ɗago sawayensu gaba ɗaya ta wantsila su gaba ɗayansu, daman haushinsu take ji gaba ɗayansu, a fusace Rumana da Angel suka taso suka cakumi Aditi, faɗa suke a junansu, wannan ta naushi wannan! Wannan ma ta kirɓa wa wannan naushi haka suka kaure gaba ɗayansu kuma kowa duka yake kaiwa ɗan uwansa, duk wanda ka samu zaka daka acikinsu... Ayush kam kallonsu ta tsaya yi a tsorace, har jikinta ya soma ɓari yana kakkarwa sosai, ta kasa ce musu ƙala saboda tana tsoron kar suyo kanta tinda taga duka suke kaiwa junansu, ɗakin yayi kaca kaca ga ferfesun kaji a kwance saman carpet, lemon da ba'a rufe ba duk sun zuzzube a ƙasin carpet, saida suka sha dambensu suka gaji kowa jikinsa yaji masa, jiki duk ba ƙarfi Aditi ta miƙe daƙer ta ciro bindigarta daman koda yaushe basa rabuwa da bindiga, kunna kunamar bindigar tayi ta saita kan Angel da shi daman tin ba yau ba tafi jin haushin Angel da kuma yawan shishigewa Junaid da take, itama Rumana tashi tayi ta ciro nata ƙaramin bindigar ta saita kan Aditi dashi, murmushi Angel tayi itama tasa hannu a aljihun abayarta ta ciro tata bindigar itama ta kunna kunamar ta saita goshin Rumana da shi, kowa duk wanda yafi jin haushi akansa ya ɗora bindigar, Rumana ta ɗora bindigarta akan Aditi, Aditi ta ɗora bindigarta akan Angel, itama Angel ta ɗora tata bindigar akan Rumana... suna haki sosai duk sun bi sun gaji, Ayush kam ganin kowa ya fidda bindigarsa ta zaro manya-manyan idanuwanta sosai, daga bisani tabi kan kujera ta kwanta sumammiya..... 𝑡𝑦𝑝𝑖𝑛𝑔✍️ 𝗠𝗔𝗧𝗔𝗥 𝗗𝗔𝗠𝗨𝗦𝗔 the wife of a tiger🐅🐅🐅🐅 𝙼𝚊𝚕𝚕𝚊𝚔𝚒𝚗 𝙰𝚜𝚖𝚎𝚎𝚝𝚊𝚑 ✍️✍️ 𝙿𝚊𝚒𝚍 𝚋𝚘𝚘𝚔 𝚌𝚊𝚕𝚕 𝚘𝚛 𝚠𝚑𝚊𝚝𝚜𝙰𝚙𝚙 09065443871 *💫💫{{N W A}}💫💫* Book two C̶h̶a̶p̶t̶e̶r̶ 005 ➡️ 006 Rumana ce ta fara sauƙar da bindigarta ƙasi tana huci ta nufi ɗakinta domin ba ƙaramin gajiya tayi ba, tana buƙatar hutawa, ganin Rumana ta tafi itama Angel ta sauƙe bindigarta tana kallon Aditi wacce har yanzu bindigarta akan Angel yake bata sauƙe ba, Angel hararar ta tayi sannan tasa hannu ta ture bindigar tana faɗin "sha sha shaa marar aikin yi.." Aditi tana haɗe da gira ta sauƙar da bindigar tana huci itama ta nufi ɗakinta, Angel gurin da Ayush take a sume ta nufa tana zuwa ta lanƙayo da hannunta ta wuyanta sannan ta riƙe kunkuminta ta ɗagata sama suka nufi upstairs a hankali suke taka matakalar har suka isa ɗakin Ayush, kwantar da ita Angel tayi a saman gadonta, sannan ta rufe mata ƙofar d'aki ta sauƙa down, ƙarewa falon tayi da kallo taga yayi kaca kaca, ɗago da kanta tayi tana kallon agogon bango ƙarfe 12 yanzu na dare, da haka Angel ta gyara falon nan tas, ga baccin da yake shirin kwasheta... WASHE GARI Junaid yana zaune a room ɗin da mommy take, kwatsam sai yaji mommy tana faɗin "burina shine naga na haɗa soyayyar Junaid da Ayush, inaso naga sunyi Aure sun hayayyafa, Allah ka cika mun burina ko bayan raina ne..." haka mommy ta rinƙa sambatun nan ido a rufe ga wasu siraran hawayen da suke faman gangaro mata, kamar wacce take mafarki.. Junaid ne ya tashi sannan ya koma bakin gadon ya zauna yana riƙe da hannunta yace "Mom! Mom!! Mom!!!..." haka yake ƙiran sunanta silently wannan ƙiran ne ya ratsa cikin dodon kunnenta a hankali take buɗe ido tana ganin dishi dishi har idon ya washe, juyo wa tayi tana kallon Junaid wanda shima ƙura wa mommy ido yayi, daga bisani ta sau masa murmushi tareda kai wa hannunta tana shirin cire oxygen dake kife a bakinta da hanci, da sauri Junaid ya riƙe hannunta yace "karki cire, bari na ƙira doctor"... yana kaiwa haka ya fice daga cikin room ɗin da saurinsa.. Doctor ne yazo duba mom, har ya cire mata oxygen, ya lanƙaye ledar jini a sama, ya gama tream ɗinta sannan ya tabbatar da yanzu ta ɗan samu sauƙi amma ba za'a sallameta yau ba.. suna cikin wannan halin saiga su Angel sun shugo su uku kowacce tana riƙe da kayan fruit a hannunta, kowa ya sha makeup sosai kamar ba su ba, suna shugowa suka nemi guri suka zaune a kujerun ɗakin tare da gaishe da mommy da jiki, Junaid ne yake lelleƙawa ko zaiga Ayush amma bai ganta ba, amma ya kasa tambayarta haka yaja baki yayi shuru... Mommy ce take kallonsu ɗaya bayan ɗaya sannan tace "ina Ayushert?..." Angel ce ta buɗi baki tace "Mom mun barta a gida saboda kanta ne yake mata ciwo..." ajiyar zuciya tayi ta lushe idanuwanta sannan ta buɗesu a hankali murya ciki-ciki tace "nidai inason ganin Ayush ɗinta, buɗe ƙofar ɗakin akayi aka shugo tareda yin sallama, gaba ɗayansu waiwaya wa sukayi suna kallon bakin ƙofa, doctor Hasheem ne da kuma Lailah tazo ziyartar mommy, ƙarisa shiga ciki sukayi suna gaisawa da mutanen wajen tareda tambayar jikin mommy, neman guri sukayi suma suka zauna, Lailah dai yanda take kallon ƴanmatan ƙasashen wajen nan da mamaki acikin ranta take faɗin "ni waɗannan su waye ne? kuma mai sukeyi a gidansu Junaid?..." da tarin tambayoyi a bakin Lailah still idonta akan su... Mommy ce ta ƙara furta "Ina son ganin Ayushh ku kawo mun ita dan Allah" Junaid yana riƙe da hannunta yace "don't worry mom, till tomorrow you will see Yushert..." mommy ta katse shi da cewa "till tomorrow? please go and find Ayush for me my son.." Junaid kawai cewa yayi "okay..." ya miƙe tsaye yana kallon gurin da su Angel suke a zaune yace "ku zauna mun da mommy zanje na taho da Yushert.." Angel ce kawai ta amsa masa amma Aditi da Rumana kawar da kansu sukayi gefe suna haɗe rai, Rumana kam har idonta ya cicciko domin tana jin baƙin cikin rashin kulawar da Junaid yake bata, tinda tazo gidansu in banda ranar data zo ba bai taɓa fakewa da ita sunyi wasu maganganu na fahimta ba... Junaid fice wa yayi daga cikin room ɗin zaije gida domin tahowa da Ayush, har zai buɗe murfin motar da su Angel sukazo da ita saiga Lailah ta fito da gudu tana faɗin "wait Ogah Junaid..." ta ƙaraso gabansa tana haki irin wacce tayi gudun nan ta gaji tace "dan Allah ka temaka ka tafi dani..." kawar da kansa yayi yana shirin shiga cikin motar ta kuma cewa "dan girman Allah Ogah Junaid..." katseta yayi da cewa "meye dalilinki nayin haka?.." har saida ƙirjinta ya buga ta zaro ido waje tace "menayi Ogah Junaid?" ita a tunaninta abunda sukayi wa Ayush ne yake tambaya, Kallonta yayi sannan yace "babu amfanin biyo ni domin nima ba daɗewa zanyi ba.." tace "eh dan Allah Ogah Junaid badon halina ba" ajiyar zuciya ya sauƙar sannan yace "ok.." tana murna da farin ciki ta buɗe gaban motar ta shiga, ita dalilin binsa tana son ganin shin har yanzu akwai sauran ƙaunar ce da Ayush ko kuma an bantse, kafin ta turo da wannan video, tana kallon gefe tayi murmushin gefen baki, tareda tarin mugunta a ranta.. bayan isowarsu gidan a falo suka tsaya Junaid ne ya soma taka matakala zai haura yaje ɗakin Ayush, itama Lailah bin bayansa tayi! ya ɗan dakata tareda juyo wa yace mata "ki dakata mun a nan falon..." turo baki tayi tareda juyawa ta sauƙa falon, tana maganar zuci "Hmmm! Ogah Junaid kenam daina zaƙewa akan Ayush domin watan dasa maka tsanar ta ya kama, wanda ko yanda take bazaka ji ɗaukin zuwa ba..." shi kuwa shigarsa ɗakin Ayush ya tarar da ita tana kwance saman gadonta sai faman sharar bacci take sakamakon maganin ciwon kai data sha, zuwa yayi waran gadon ba magana haka ya kama ƙafarta ya jawota gabansa sannan ya miƙar da ita tsaye yakai hannunsa ya ɗago ƙafarta yayi mata ɗaukan luɗa ya nufi bakin ƙofa da ita.. ita kuwa Ayush a gigice ta farka sauran kaɗan tayi ihu takai idonta kan Junaid ganin shine yasa tayi shuru tana kallonsa cike da mamaki, tana lumshe ido tareda buɗesu a hankali baccin bai gama isar ta ba, har suka sauƙa downstairs Ayush tana manne a faffaɗar ƙirjin Junaid yanda yake ɗauke da ita, saida ya sauƙo falo tukun ya sauƙar da ita, Lailah ganin su a haka yasa ta miƙe tsaye da sauri tana daga zaune tana kallonsu cike da takaici da kuma tsananin mamaki a ranta tace "kutt amma Ogah Junaid sam bashida zuciya wallahi, sauna ne shi! duk bonsa shi datayi a cikin mutane amma ya kasa yin zuciya dubi yanda ya cacumota kamar wata jaririya..." Junaid ne ya jawo Ayush jikinsa bayan ya sauƙe ta, yasa hannu ya tallafo haɓarta suna kallon juna yace "meya hanaki zuwa hospital?.." shuru tayi bata bashi amsa ba sai binsa da kallo take, "tambayarki nake meyasa baki koma asibiti ba?.." nan ma shuru tayi ta kasa cewa komai sai ido, ransa ne ya sosu ganin bata bashi amsa ba, yana kallon cikin eyes ɗinta yace "Yushert ina sauraronki, meye dalilinki na ƙin zuwa hospital?.." still tayi masa shuru, cike da takaici ya dafe goshinsa tareda rufe eyes ɗinsa ya saketa, saida ya juya bayansa kafin ya sake juyowa tareda darara mata wani irin gigitaccen tsawa.. ba Ayush ba hatta Lailah wacce take tsaye tana sauraronsu saida ta tsorita sosai tasa hannu ta toshe kunnuwanta tsabar ƙarfin tsawar jikinta har ɓari yake, Ayush kuma tafiya tayi luuuu tayi baya zata faɗi yayi saurin taro ta ya kwantar da ita saman ƙirjinsa, ba ƙaramin tsorita tayi ba, ƙirjinta yayi wani irin bugawa lokaci guda kuma ta nemi numfashinta ta rasa, ƙara ɗaukarta yayi ya kalli gurin da Lailah take yace "zaki iya tafiya?.." jin irin tambayar da yayi mata yasa ta sake jikinta tareda narkewa ta dafe goshin ta tace "Ogah Junaid bazan iya tafiya ba, hajijiya nake jiiii.." tayi maganar a shagwaɓe tareda faɗuwa ƙasin carpet ta lumshe idonta, ganin makirci take son masa yaja dogon tsuka sannan ya fice da Ayush a hannunsa yaje ya buɗe murfin mota ya kwantar da ita a seat back sannan ya koma falo, Lailah harta buɗe idonta tana jin motsinsa ta rufe idonta da sauri, yana zuwa kuwa ya riƙo ƙafarta ɗaya ya ringa janta a ƙasi har suka fita daga falon yana janta, ganin zai ƙoƙe mata gadon bayanta yasa ta buɗe ido tana faɗin "wayyo Allah na Ogah Junaid bayana, dan Allah ka sake mun ƙafa zan taka da sawaye naaaa" tana maganar kamar zatayi kuka, shi kuwa bai daina janta a ƙasa ba har saida suka zo daf da motarsu tukun ya sake mata ƙafarta, ta tashi tana dafe bayanta data kurzu da floor ɗin gidan, jikinta ne ya soma mata ciwo daƙer da shige gaban mota ta zauna tana matsar hawaye.. Junaid figar motarsa yayi ya fice daga gidan da gudun gaske ko kallon yanda Lailah take baiyi ba, fuska a haɗe ba annuri... ☆☆☆☆☆ A masarautar sarki Raamud! Uma Bara'at ce take kwance saman ƙirjin sarki Raamud tana kuka tareda faɗin "Ayush ta bani kunya wallahi, ban taɓa tunanin zata yi haka ba, yanda ta nuna tana son Junaid nayi mamaki sosai.." Sarki Raamud bubbugar bayanta yake a hankali yana rarrashinta yace "kiyi haƙuri mana BB, idan kinga haka akwai laifin da yayi mata, amma yanda Ɓingel take da haƙuri zaiyi wuya ta aikata hakan ba tareda dalili ba, ya kaita maƙura shiyasa..." Uma Bara'at ɗagowa tayi tana kallonsa tace "haba shugaba a cikin dubban mutane fa tayi masa haka, aiko meyayi mata bai kamata ta yanke wannan hukunci ba, kaide kawai kana goyon bayan Ɓingel ɗinka ce shiyasa.." ta maida kanta ta kwantar saman ƙirjinsa, yace "to ke meyasa zaki damu haka bayan kinsan zasu dawo su ƙara haɗewa, ai bazasu rabu ba saidai kuyi ta jin kunya.." Uma Bara'at tace "hmmm! tayi wa kanta ai, ni badan NARASIMHA ya bani zoben da zan ɓace naje gurin taron ba ai da bazanje naga wannan takaicin ba, kasan Narasimha yana kallonsu duk abunda suke yi..." Sarki yace "eh mana ba shi bane yazo ya sanar mana baikon su ɓingel ba..." bai ƙarasa maganar ba yaji Bara'at tana yunƙurin amai, kafin ya buɗe baki yayi magana har ta tashi da gudun gaske ta nufi toilet tana kwarara amai, biyo bayanta yayi yana faɗin "BB meyake faruwa ne? meya sameki?.." ɗagowa tayi tana haki ya riƙo hannunta ya kuma cewa "BB bakida lafiya ne? muje mu gun Narasimha ya duba ki yaga meyake damun ki, kinji ko.." wuce wa tayi ta gefensa tace "ba wani abu bane kawai ɗan zazzaɓi nake ji ne..." shugo wa bedroom sukayi yanata binta akan suje gurin Narasimha ya bata magani amma furr taƙi yadda, ganin bazata je ba yasa hannu ya ɗauketa ya fice da ita, wurwurga ƙafafuwa take tana faɗin "ni ka sauƙe ni wallahi bazan je gurin Narasimha ba, ya cika bala'i, ni ka sauƙe niiii..." a falo suka tarar da Narasimha tsaye, a lokacin ya sauƙeta ganin Narasimha a falon masarauta, gaishe shi Sarki yayi ya kuma amsawa, Baba Narasihma juyowa yayi yana kallon Bara'at da ƙananun idanuwansa da fuskar biri jiki duk gashi yace "keee wato nine mai bala'i ko? dan uwar uwarki ko mijinki bai isa ya ce ni inada bala'i ba, daman wancan munafukar ɗiyar takin taurin kanki ta ɗauko har ta bijirewa baikon Junaidu saboda ita ƴar banza ce, saboda ita munafuka ce tana son Junaidu amma ta rufe ido ta wulaƙanta shi, toh daga ke har ɗiyar takin da mijin nakin duk kunci uwar uwarku ƴan gwafar uba, da bakya so na duba ki to cikin ƴan biyu gare ki ƴar banza kawai...." yana kaiwa nan yayi wuce warsa yana tafiya da ƴar jelar bindinsa, gashi a tsaye kamar mutum amma suffar biri ne dashi, kamar su ɗaya sak da biri, yana tafiya yana tokara sandarsa.... *MASHA ALLAH BACCI NAKE JIII SAI GOBE INSHA ALLAHU ZAN CIGABA MUKU DA TYPING...* 𝑡𝑦𝑝𝑖𝑛𝑔✍️ 𝗠𝗔𝗧𝗔𝗥 𝗗𝗔𝗠𝗨𝗦𝗔 the wife of a tiger🐅🐅🐅🐅 𝙼𝚊𝚕𝚕𝚊𝚔𝚒𝚗 𝙰𝚜𝚖𝚎𝚎𝚝𝚊𝚑 ✍️✍️ 𝙿𝚊𝚒𝚍 𝚋𝚘𝚘𝚔 𝚌𝚊𝚕𝚕 𝚘𝚛 𝚠𝚑𝚊𝚝𝚜𝙰𝚙𝚙 09065443871 *💫💫{{N W A}}💫💫* Book two C̶h̶a̶p̶t̶e̶r̶ 007 ➡️ 008 Bayan shigar su Junaid cikin hospital kafin su fito daga cikin motar ya kalli Lailah yace "get out" juyowa tayi tana kallonsa kamar wacce zatayi kuka ta ƙara juya bayanta tana kallon Ayush dake kwance a bayan seat, buɗe baki tayi zatayi magana ya darara mata tsawa "i said get out..." a tsorace tayi saurin buɗe murfin motar ta fice, kai tsaye compound na asibitin ta nufa tareda juyo wa tana kallon motarsa ko fitowa baiyi ba, yana daga cikin motar ya ɗauki robar faro mai ɗauke da ruwa a ciki ya since murfin tareda tsiyayar ruwan a tafin hannunsa yana watsa wa Ayush a fuska, a gigice ta tashi zaune tana maida numfashi sama-sama tana juyar da eyes ɗinta tana kallace-kallace acikin motar, muryarsa taji ya daki dodon kunnenta da sauri ta kalli yanda Junaid yake a zaune a front car, shima kuwa kallonta yake ta cikin madubin motar ba tareda ya juyo ba yace "ki dawo gaba ki zauna.." a tsorace take binsa da kallo ta kai hannu zata buɗe murfin motar ya katseta da cewa "ba sai kin buɗe ba, ki hauro ta sama ki zo.." tashi tayi ta zuro ƙafarta ta gaba tana shirin dirƙowa har sai da ta dafa ƙafaɗarsa tukun ta samu ta zauna suna jere da juna, "meyasa baki biyo su Angel kunzo duba mamana ba? ko saboda ba mahaifiyarki bace shiyasa baki damu da jinyarta ba, yanda ta damu dake ke baki damu da ita ba why...." hawaye ne suka fara zarya a saman kuncin ta tasa hannu tana gogewa baki na rawa tace "sanin abunda ke zuciyata sai Allah, amma duk abunda kace dai daine, amma Allah na gani yanda nasa mommy a raina ko mahaifiyata bansata a raina kamar haka ba..." katseta yayi da cewa "ƙarya kike, da kin damu da ita da bazaki so ganin ɓacin ranta ba, hasali ma saboda ke ta kwanta jinyan nan.." dogon numfashi yaja sannan ya juyo yana kallon ta ya kuma cewa "Yushert ki sani abaya kin shiga raina har na fara sonki amma a yanzu babu wannan so, domin ni bana son maso wani! muna tare a gida ɗaya amma banaso ki ƙara kusantar yanda nake domin na rigada na yanke alaƙarmu, Allah ya zaɓa miki wanda ya fini kuma wanda zai nuna miki ƙauna fiye da wanda na nuna miki a baya...." yana kaiwa ƙarshe ya buɗe murfin motarsa yayi ficewarsa, ita kuma rufe fuskarta tayi da hannayenta biyu ta fashe da wani irin matsanancin kuka mai ƙona zuciya, sai da tayi kukanta mai isarta tukun ta share hawayen fuskarta idonta yayi lufu-lufu ta buɗe murfin motar itama ta nufi cikin asibiti tana kakkare fuskarta saboda kar asan kuka tayi, a hanyar shigarta ciki ta haɗu da Doctor Hasheem yana tafowa suka yi kucuɓus, ƙiran sunanta yayi cool "Ayushert! kinzo ki ne.." ɗaga masa kai kawai tayi tana sunkuye da kanta, hannu yasa ya tallafo fuskarta ya ɗago da fuskar sama suna fuskantar juna yace "meya faru dake kike kuka?.." girgiza masa kai tayi tace "babu komai" murya ciki-ciki yace "ke da Junaid koh?.." kallonsa kawai take ba tareda ta bashi amsa ba, adaiden lokacin da shi kuma Junaid ya tafo, ya tarar dasu a haka Doctor Hasheem yana riƙe da haɓarta, wuce wa yayi ta gefensu ba tareda ya ce musu komai ba, Ayush da sauri ta waiwaya tana bin bayan Junaid da kallo sabon kuka ne ya sake kuɓuce mata, Doctor Hasheem ya riga da ya gano matsalar riƙe hannunta yayi yana faɗin "muje na kaiki ɗakin da Mommy take, amma ki daina kuka bason ganin hawayenki nake ba kuma still zaki tayarwa mommy da hankali kinsan tana fama da heart pain..." Ayush dakatar da kukan tayi ta goggoge hawayen fuskarta sannan suka nufi room ɗin da mommy take... bayan jigarsu cikin room ɗin da gudu Ayush ta nufi yanda mommy take a kwance, itama mommin rungumar Ayush tayi a jikinta sosai tana ɗan bubbugar bayanta ganin yanda Ayush ta fashe da matsanancin kuka, Lailah tsuka taja ta miƙe tsaye daiden lokacin suka haɗa ido da Aditi wacce jin tsukar yasa ta juyowa tana kallon Lailah, a fusace Aditi ta miƙe taje gaban Lailah ta kirɓa mata naushi a baki, kafin kace mai jini ya fara ambaliya a bakin Lailah, hakan ma Aditi ta ƙara zabga mata mari har sau biyu a fuskarta tana faɗin "ni sa'ar ki ce da zaki mun tsuka? na fahimci tinda kika zo kanki yake gigiwa..." duk wannan maganar Aditi ta juyar da shi zuwa yaren turanci saboda Lailah tafi ganewa, Lailah kama bakinta tayi ta fara kwarara ihu a wajen jinin bakinta duk ya wanke mata hannu, Doctor Hasheem ne ya riƙo Lailah yana kallon Aditi yace "ya haka baiwar Allah metayi miki?.." Aditi ta kalle shi sannan tace "baka ji menace bane?..." kafin Doctor Hasheem ya sake yin magana Lailah ta katse shi da cewa "wallahi tallahi Yaya bada ita nake ba, kawai dai zaluncin ta ne a kusa, ni ba abunda nayi mata ta fasa mun baki naaaa..." kuka take sosai tana riƙe da bakin, Doctor Hasheem yace "it's okay Auta muje na wanke miki kinji koh, don't worry.." har sunyi kusan fita Lailah ta juyo tana kallon Aditi tace "munguwa, azzaluma, bad girl..." Aditi ranta yayi mungun ɓaci dajin kalaman Lailah da gudu ta taro su tareda fincikar Lailah tayi wurgi da ita ciki, ta ɗagata sama ta ƙwanɗarata a ƙasin tiles, Lailah kuka ɗaya tayi ta suma a wajen, Doctor Hasheem a fusace yayo kan Aditi, da sauri Aditi ta fitar da bindigarta ta saita masa a goshi tareda kunna kunamar bindigar tana faɗin "idan ka sake matsowa saina fasa maka kayi da harsashi, kuma idan na kashe ka na kashe banza a bola, i am a girl army..." ta ciro katinta ta nuna masa still bakin bindigar yana saite akan sa, Doctor Hasheem ganin ita soja ce yasa ya risina ya ɗaga hannunsa sama yana faɗin "kiyi haƙuri ban saniba, insha Allahu za'a kiyaye gaba.." sauƙar da bindigarta tayi ƙasa tana hura hanci ta nemi guri ta zauna, shi kuwa a tsorace ya ɗauki Lailah suka yi waje, Angel tana hararar Aditi tace "meye haka kikayi Aditi? anya kuwa kinada hankali?..." kafin Angel ta rufe baki Aditi ta kwasheta da mari tana huci, Angel zabura tayi zata miƙe tsaye domin ɗaukar fansa mommy tayi saurin dakatar da ita tareda cewa "a'ah Angel kiyi haƙuri ki barta dan Allah, kindai san halinta daman bata da haƙuri ko kaɗan, kar kema ki biye mata kinji ko?.." komawa tayi ta zauna tace "Allah mom da kin barni na koya mata hankali wallahi..." mommy tace "ke dai ki shareta kawai..." Aditi shuru tayi tana jinsu amma saidai da hausa suke maganar bata jin yaren.. Rumana kam tana zaune ko kallon yanda suke bata yiba, saima ɗaukar jakarta datayi ta miƙe tsaye tana faɗin "let me go home, i need to rest.." Mommy ce kawai ta amsa mata tace "ok shikenam Allah ya kiyaye hanya sirikata.." ficewa Rumana tayi tana taku da takalminta mai shegen tsini... Ayush kam tana kwance akan ƙirjin mommy tana kallonsu sai gani sukayi Aditi ta janyo ƙafar Ayush zuwa ƙasa tana cewa "kina kallon mom ba lafiya kin wani kwanta mata a jiki, ke jaririya ce? ki tashi ki zauna ko kuma nayi miki dukan tsiya a waran nan..." da sauri Ayush ta tashi zaune kamar zatayi kuka, ita tsoronta kar tayi mata dukan da tayiwa Lailah wanda har ta suma, Angel tana kallon Aditi daga bisani kuma ta girgiza kai tana mata kallon marar hankali ba tareda tace komai ba ta kawar da kanta gefe... Itama mommy kallon Aditi kawai take tana murmushi aranta tana faɗin "oh haka ke kuma kike da masifa, Allah ya shirye ki..." suna cikin wannan halin saiga Junaid ya shugo hannunsa riƙe da ledoji na siyayya daya yo, yana shugowa yace "lafiya kuwa yana ganku kunyi shuru..." Angel ce ta buɗe baki zatayi magana ta sanar masa abunda Aditi tayi, mommy tayi saurin tarar yawunta gurin cewa "babu komai.." yace "ha'a yana ji kuna haɗa baki waran yin magana?.." saida ya ajiye ledojin hannunsa akan glass table tukun ya kalli yanda Angel take yace "my Angel meya farune?.." turo baki tayi tace "ina dai Aditi ce.." tayi maganar tareda nuna ta, Aditi jin Angel ta ambaci sunata ta waiwayo tana mata kallon up and down tace "what's wrong..." itama Angel hararar ta take tace "bansani ba munafuka.." Aditi da sauri takai hannu zata naushi Angel, Ogah Junaid yayi saurin riƙe mata hannu yana faɗin "ke ke ke kinga matsala ta dake kenam Aditi, saurin kaiwa hannu meye matsalarki ne kam?..." fuzge hannunta tayi tana fushi ta miƙe tsaye sannan tace "ai daman kafi sonta, shiyasa kake nuna warayya a tsakanin mu..." tana kaiwa karshe tayi ficewarta a cikin ɗakin, Junaid yana ƙiranta amma ko ta waiwayo haka tayi tafiyarta, Angel itama surutan ta take tana faɗin "ai wallahi da ka barta ta naushe ni saidai uwarta ta haifi wata amma babu abunda zai hana na harbeta.." Junaid yana jin abunda Angel take faɗa amma ya sharar da ita sai cewa yayi "ina Rumana?..." mommy tace "ta tafi gida.." sauƙar da ajiyar zuciya yayi tareda kaiwa idonsa kan Ayush wacce tin shugowar Junaid kanta ke ƙasi ta kasa ɗagowa... Mommy kallon yanda Angel take tayi tace "Angel da kin koma gida kema kinyi mana girki saboda masu zuwa ganin jikina, nima anjuma kaɗan zan koma gida, ai na samu lafiya...." Angel ta amsa mata da "toh mommy sai kun dawo, bari na hanzarta na koma gidan.." miƙe wa Àngel tayi tareda yi musu sallama tayi tafiyarta.. Mommy ta kalli Ayush tana shafa kayinta tace "Dota waya taɓa mun ke naga kamar kinyi kuka?..." a hankali Ayush tace "babu komai mommy, kawai na damu da ganinki a asibitin nan a mazannin marar lafiya..." murmushi mommy tayi sannan tace "ba komai Ayush ai naji sauƙi yanzu kam sai komawa gida.." Ayush tana hawaye ta kalli mommy tace "dan Allah mommy kiyi hakuri, na wargaza miki lissafi bansan ke kika haɗa baikon nan ba, da bazan bijire ba kuma a lokacin a tsorace nake da Yaya Janaid...." mommy ce ta katseta da cewa "kinga kiyi shuru maza kar kina tunowa da abunda ya wuce, idan har Junaid mijinki ne babu makawa sai anyi auren nan, idan kuma ba shi bane mijinki ba ko mai mukayi baza'a taɓa yin auren nan ba, don haka mahakurci mawadaci ke dai ki cigaba da addu'a, insha Allahu Allah zai zaɓa miki wanda yafi alkhairi my Dota..." Junaid yana zaune akan kujerar d'akin yana jinsu amma baice musu komai ba, sai ma daddannan wayarsa da yake yi.... Bayan wuni guda Angel ta kammala girkinta ta gyara gidan tsab, yanke shawara tayi cewar zata je gurin swimming pool taje tayi wanka acan, zagayawa tayi ta baya, wani ɗanƙareren swimming pool ne ya tsaru sosai, ruwan mai colour green, tarar da Rumana tayi a wajen tana zaune a kujerar wajen da ɗan ƙaramin table a gabanta ga lemuka a jere, saidai babu kaya ajikinta daga ita sai ɗan pant da kuma rigar breziya, jiki fari sol da ita sai karatun wani ɗan littafi take a hannunta.... ta ɗayan ɓangaren kuma Àdhiti ce a cikin ruwa da breziya sai pant a jikinta sai wasan ruwa take, tana tafiyar kifaye... Àngel ɗan tsuka taja ganin duk sun tare duk anan wajen ko aikin gidan basu tayata ba, da kamar zata juya kawai ta fasa itama ta cire kayan jikinta ta zauna daga ita sai short nicket, tana zuwa tayi tsalle ta faɗa cikin ruwan saida Aditi ta nutse cikin ruwan sosai tsabar tsallen da tayi a cikin ruwan, itama Rumana tana zaune agefe tana karatun littafin ta taga ruwa duk ya jiƙe littafin sakamakon tsallen da Angel tayi a cikin ruwan, Rumana rarumar glass cup tayi akan table saida ta saita kan Angel tukun ta wurga mata a tsakiyar kanta, da sauri Angel ta juyo tana riƙe da kanta tace "kuturun uban cannn...." bata ƙarasa maganar ba taji Aditi ta shaƙo wuyanta ta baya, daƙer Angel ta samu ta kuɓuce a hannun Aditi ta fito tana maida numfashi ta nufi gurin da Rumana take a zaune ta hankaɗata ƙasi ita da kujerar, Aditi ce itama ta fito daga cikin ruwan da gudu ta nufo yanda Angel take ta kamata da kokuwa suka fara kirɓawa juna naushi, Rumana itama tasowa tayi ta shiga suka fara faɗa kowa wanda yake jin haushi yake daka, a wannan lokacin Aditi tayi nasarar gurɗa ƙafar Angel sakamakon kwantar da ita datayi ƙasa ta kama ƙafarta ta murɗe mata shi, har saida Angel ta saka ƙara sosai tana kwance ta kasa motsa ƙafar, Aditi ganin Rumana tana ƙoƙarin cakumo ta yasa ta zari ƙwalbar lemo ta rausawa Rumana a goshi, nan da nan jini ya fara kwararowa daga goshin Rumana, baturen mutum da baya son ganin ciwo a jikinsa hakan yasa Rumana faɗuwa ta sume a gurin... Aditi tashi tayi tana huci tareda faɗin "ku taso mana inadai kun raina ni ko? toh zan nuna muku ni mahaukaciyar soja ce, ku taso..." tana haki da ƙarfi-ƙarfi tana fitar da maganar daƙer kamar wacce tayi aikin ƙarfi.. Junaid ne yazo gurin yana faɗin "ku kuma kunzo nan duk kun tare guri ɗaya kun bar falo babu kowa....." bai kai ƙarshen maganarsa ba yaci karo da Rumana kwance ko motsi babu ga kuma jini ya wanke mata fuska, yakai idonsa kan Angel sai juye-juye take tana riƙe da ƙafarta tana kuka, kallon yanda Aditi take a tsaye tana huci yayi bakinsa na kakkarwa tsabar ɓacin rai yace "meya faru dasu?..." juyowa tayi tana fuskantarsa hannu a dunƙule tace "nine nam nayi aiki akansu, idan kuma kaima kana son tabbatar da aikina kazo ka ga..." tana tsalle irin na ƴan dambe... da sauri yayo kan Rumana ganin tafi jikkata, da gudu Aditi ta shige gabansa tana faɗin "babu wacce zaka taɓa" tureta yayi gefe sannan yasa hannu zai ɗauki Rumana sai ji yayi Aditi ta kirɓa masa naushi a baya, cikin ɓacin rai ya juyo tareda zabga mata mari, zata kawo masa naushi kuma du ya riƙe hannayenta biyu da hannu ɗaya ya zaro ƙafafunta da ɗayan hannun ya cillata cikin ruwan swimming pool, ya juyo ya ɗauki Rumana a kafaɗarsa, sannan ya miƙawa Angel hannu ta tashi daƙer ya riƙe kunkuminta da ɗayan hannunsa, ɗayan kuma yana riƙe da Rumana yanda ya saɓata a kafaɗa haka suka nufi falon gidan, Ańgel tana ɗingishi daƙer take takawa.. suna shiga cikin falon mommy da Ayush duk suka miƙe tsaye daga zaune, Mommy cike da mamaki tace "subhanallah ya haka kuma?..." ganin yanda suke ba kaya a jikinsu ko wacce daga pant sai breziya, Ayush kam rufe idanuwanta tayi da hannayenta biyu, Junaid ne yace "mom please ki biyo mu can medicine room kiyi treat ɗinsu, sunji rauni sosai...." Mommy ce ta taɓa Ayush tana faɗin "kije ɗakunansu ki dubo musu kayan sakawa yanzun nan.." tana kaiwa karshe tabi bayan Junaid da sauri... Bayan Ayush ta jido musu kayan sakawa tana fitowa falo saiga Aditi ta shugo falon ita da kayanta a jikinta domin tin acan ta sanya su, tana zuwa ta wuce ɗakinta tana jan zuciya ga idonta yanda sukayi jaa..... 𝑡𝑦𝑝𝑖𝑛𝑔✍️ 𝗠𝗔𝗧𝗔𝗥 𝗗𝗔𝗠𝗨𝗦𝗔 the wife of a tiger🐅🐅🐅🐅 𝙼𝚊𝚕𝚕𝚊𝚔𝚒𝚗 𝙰𝚜𝚖𝚎𝚎𝚝𝚊𝚑 ✍️✍️ 𝙿𝚊𝚒𝚍 𝚋𝚘𝚘𝚔 𝚌𝚊𝚕𝚕 𝚘𝚛 𝚠𝚑𝚊𝚝𝚜𝙰𝚙𝚙 09065443871 *💫💫{{N W A}}💫💫* Book two C̶h̶a̶p̶t̶e̶r̶ 009 ➡️ 10 Junaid da sauri ya fito falo ya nufi yanda frig yake ya buɗe tareda ɗaukar ruwan faro mai sanyin gaske ya koma yanda ya fito, ita kuma Ayush bayan ta kai musu kayan komowa tayi falon ta nemi guri ta zauna tayi tagumi kamar wata marainiya, bayan wasu mintuna saiga mommy ta fito hannunta riƙe dana Angel tana ɗingishi, sai Rumana dake tafe duk goshinta an zagaye da bandeji, shi kuma Junaid yana biye dasu a baya, Ayush ganinsu yasa ta miƙe da sauri tana kallonsu tareda faɗin "sannunku ya jikin nakun?.." Angel ce ta amsa murya ciki-ciki, ita kuma Rumana ko ƙala batace ba haka ta wuce ɗakinta, mommy da Angel da kuma Junaid neman guri sukayi suka zazzauna, itama Ayush ɗin zama tayi idonta akan Junaid domin bata gajiya da kallonsa, shima yana lura da kallon da take masa saidai baya bari su haɗa ido, gaba ɗaya wajen yayi tsitt ba wanda ya kula kowa acikin su sai Angel ce data kalli yanda Junaid yake ta faman press phone ɗinsa tayi gyaran murya, murya a sanyaye tace "my Man ya batun sarki Raamud ne?.." ɗagowa yayi yana kallonta yace "baki sanar mun komai akansa ba har yanzu.." kallon yanda mommy take Angel tayi sannan tace "munyi bincike sosai akansa sannan mun gano cewa matar data zauna daku a matsayin ƴar aikinku matarsa ce, wato Bara'atu..." a zabure Junaid ya miƙe tsaye tareda faɗin "whatttt...?" itama mommy saida ta girgiza dajin wannan batun, Ayush ido ta zaro waje tana binsu da kallo, zuciyarta kuwa haka yake bugun uku-uku, Angel tana bin Junaid da kallo tace "ba abun mamaki bane dan ance matarsa ce, saboda bakinsu ɗaya kuma shi ya turo ta nan gidan domin ta shiga cikin rayuwarku ta misguna muku" ta kuma cewa "ka zauna mana mu ƙarasa maganar..." jiki a sanyaye ya zauna yana cewa "ina jinki Angel.." ta kuma cewa "yarinyar da Bara'at tabar gidan nan da ita ƴarsu ce kuma sunanta Mayushat, a yanzu dai basa tareda yarinyar kuma gaskiya bamu gano a yanda take ba, amma guaranty Sarkin matsafa yana tareda matarsa Bara'atu a halin yanzu, sannan bincike ya nuna cewa yanzu babu wani tasirin da suke dashi na tsafi, zamu iya kai musu farmaki a koda yaushe, tawagar mu tana kan shirinta domin zuwa farmakar su, an sanar wa sojojin nan nigeria da kuma na pakistan da sojojin china da na UK da US duk akan su shirya ranar 5 ga watan November 2023, next week kenam, jirgin land army da kuma airpos na Nigeria zai tashi a ranar Monday, zamu fara shirin mu daga yau friday zuwa monday domin damu za'ayi wannan tafiyar, sai kuma mu dage da addu'a domin a tafiyar yaƙin namun bamu san mai zamu tarar ba, bamu san waye zai mutu ba waye kuma zai rayu..." Junaid kallon Angel yake cike da baƙin cikin sarki Raamud a cikin zuciyarsa, buɗe baki yayi yace "a shirye nake dana yaƙe shi, kuma ni zan zamo ajalinsa..." Angel ce ta katse shi da cewa "a'a shuwagabannin mu basu bada umarnin a kashe shi ba, da ransa suke son ganinsa.." Junaid miƙewa tsaye yayi yana darara wa Angel tsawa tareda faɗin " i will kill him with his wife, babu wanda ya isa ya dakatar dani, sai dai nayi sanadiyar rasa aikina da kuma rayuwata, amma saina kashe mutumin daya azabtar da rayuwata, saina kashe matar da tayi sanadiyar mutuwar mahaifina, sannan kuma bazan taɓa ƙyale ɗiyarsu ba, saina nemo ta a duk yanda suka ɓoyeta..." yana kaiwa haka ya bar falon ya haura upstairs... Ayush tana zaune jikinta ne ya hau ɓari tana rawar sanyi, wani irin zazzaɓi ne mai zafin gaske ya rufeta, tinin hawaye har ya cicciko mata, zuciyarta yana bugu da ƙarfin gaske, ganin kuka yana shirin kuɓuto mata yasa ta tashi da sauri itama ta haura upstair zata koma ɗakinta, tana shiga kuwa ta danna sakata a ɗakin ta faɗa saman katafaren gadonta tana rera kuka na gaske.. Junaid kuwa toilet ya shige, ruwa ya kwara a kansa yayi wanka shap-shap ya fito ya shirya cikin wandon soja da farar t-shirt, ya zura takalminsa sahu ciki irin na sojoji, ya feffesa turare sannan ya fice da sauri ya sauƙa down stairs, Mommy da Angel ne suka miƙe tsaye a zabure ganin Junaid yana shirin ficewa, Mommy tace "ina zaka je Junaid?..." juyowa yayi yace "zanje headquarters ne domin na tantance ƙarfafan sojojin da za'ayi tafiyar dasu ba lusarai ba..." yana kaiwa haka yayi ficewarsa, a gigice yaje ya shige motarsa ya fizgeta da gudun gaske, maigadi daman tin fitowar Junaid yayi saurin buɗe masa gate... Mommy tana daga tsaye ta kalli Angel da damuwa a fuskarta tace "wallahi Angel ina tsoro kar wani abu ya cutar mun da yarona, har ina ne ƙasar da zakuje?..." Angel ta sauƙe ajiyar zuciya tana hura iskar bakinta tace "ki kwantar da hankalinki mom insha Allahu ba abunda zai faru da Junaid, ai jarumin namiji ne ba'a yaƙarsa sai dai ya yaƙi mutum, kuma ƙasar da za'a hallaru acan domin gudanar da yaƙin can ƙasar California ne, toh masarautar babu kowa yanzu haka sai su, babu mutane ko ata gefensu ne, waran dai ya kasance daji ne..." Mommy tace "toh shikenam Allah dai yasa aci nasara akan su, a kamosu dumu-dumu..." Angel tana murmushi tace "ai zamu ci nasara tinda sojojin da zasu hallara ba kaɗan bane, sojoji ƙasashe daban daban ne zasu zo domin gudanar da farmaki... Ayush tashi tayi daga kwance tana zazzagaya cikin room ɗinta tareda faɗin "innalillahi wa inna'ilahi raju'un, shikenam iyayena nashiga uku nah, Allah ka karemun iyayena, taya zan sanar musu cewar su tafi? ta ina zan sanar musu cewar su gudu kafin ranar? ga yanzu babu tsafin da zanyi magana dasu ta cikin madubi, meye ake shirin aikata wa iyaye nane?..." tana magana tana kuka sosai gaba ɗaya ta susuce.. Around 6 o'clock bayan anyi sallar mangrib Angel ce ta fito ta gama shirya musu dinner na kayan abinci, sai data kammala tsab tukun taje ɗakin mommy ta tarar da ita akan sallaya ta idar da sallah, Angel ta mata magana akan ta fito su ci abinci, mommy ta amsa mata da "toh" sannan ta fice a ɗakin ta nufi upstairs taje tana kwankwasa wa Ayush, saida ta ɗan juma a tsaye kafin Ayush tazo ta buɗe mata, idon duk ya kukkumbura, Angel tana ganinta tace "subhanallah Ayush meya sameki ne haka?.." tana motsa baki daƙer tace "babu.." Angel tace "kin fiye kuka da yawa, zakije ki sawa kanki ciwo ne, ke kullum kina cikin damuwa ba wargi, toh idan kika ce zaki biyewa Junaid ne mutuwa zakiyi murus domin Junaid asalin miskilin namiji ne, baya nuna damuwa akan abu, shawarar da zan baki shine ki zamo mace mai class, idan yaga bakya shiga harkarsa to shida kansa zai nemeki, amma yana ganinki kullum a haka duk saboda shi toh ya ringa gallaza miki kenam, ai namiji ba'a nuna masa tsananin so, kuma ma ai ke kika jawo agun baiko kika fetsare ido kika ce bakya sonsa alhalin son sa da kikeyi yafi wanda yake miki, ai yanzu ba maganar kuka, ki fito muyi night dinner..." lips ɗinta ne yake kakkarwa daƙer tace "ni akawo mun cikin ɗakina..." Angel tace "a'a wallahi ki fito yanzun nan muci acikin mutane, Allah ciwon zuciya zai kamaki Ayush, na gaya miki ki fito yanzun nan, mommy tana jira..." tana kaiwa karshe tayi tafiyarta, saida ta duba room ɗin Junaid taga bai dawo ba har yanzu tukun ta sauƙa downstairs, ta tarar da mommy har ta fito, mommy tace "me kikeyi ne tin ɗazu?.." tace "wallahi mommy na tsaya agurin Ayush ne, tana nan fitowa itama.." Mommy ta kuma cewa "Junaid ya dawo?." tace "a'ah mommy.." Mommy tace "toh shikenam kibi ɗakunan sauran kice su fito.." ta amsa mata tareda nufan ɗakin Rumana tana kwankwasawa cikin ƙanƙanin lokaci saiga Rumana ta buɗe daga ita sai gajeran wando na sojoji ajikinta da black t-shirt, tana hararar Angel tace "ya akayi?.." Angel juyawa tayi tareda faɗin "ki fito aci abinci inji mommy..." Rumana bata koma ciki ba haka ta fito gaba ɗaya ta nufi gurin dinning table tana press ɗin wayanta, goshi kuwa duk anzagaye da bandeji... Angel zuwa ɗakin Aditi ta nufa itama ta kwankwasa mata! da sauri aka buɗe ƙofar tana masifa ganin Angel yasa ta turɓune fuska tace "menene kodai dukan ne bai isheki ba?.." Angel tace "ni ba masifa ce ta kawo ni ba, kizo inji mommy aci abinci..." tana kaiwa nan tayi juyawarta itama waran dinner ta nufa ta zauna a kujerar kusa da mommy, itama Ayush fitowa tayi saida ta wanke fuskarta tukun ta zauna a kujerar kusa da Rumana, saiga Aditi itama tazo ta zauna a ɗayan kujerar gefen Angel ta toshe da earpice a kunnenta, Angel ce ta buɗe kulolin gurin tana zuzzuba musu alokacin ne Junaid shima ya dawo, yana shugowa shima ya nufi gurin cin abincin domin wani irin yunwa yake ji, zama yayi a kujerar da yake fuskantar Aditi... suna cikin cin abinci ba wanda yake kula kowa, ita kam Ayush bata ci sai faman juya spoon take, Mommy ce ta ɗago tana kallonta tace "Ayush lafiyarki kuwa, tin ɗazu nake nura dake ba wani abincin kike ci ba, meya faru dake?.." girgiza kai tayi tace "babu komai.." ta fara tusa abincin daƙer a bakinta tana ci kamar bazata ci ba... suna cikin wannan yanayin sai wayar Rumana ta fara rurin ƙira, ganin screen ɗin wayar tayi tace "oh god.." duk kallonta sukayi daiden lokacin ta kara a kunne tana faɗin "hello Ogah Sir..." saiji sukayi tana cewa "okay Sir, yes Sir, yes Sir, Okay Sir, thank you Sir..." ta sauƙe wayar tana sauƙe numfashi, tana kallon mutanen wajen ɗaya bayan ɗaya, Junaid ne ya kalleta yaga yanayinta har ya sauya yace "what's wrong with you?.." ta kalle shi tace "yanzu zan tafi airport zuwa cikin dare zan isa Australia, ana neman mu agurin aiki wai akwai yaƙin da zamu fita next week zamu je mu fara shirye-shirye..." murmushi Junaid yayi sannan yace 'ai daman nasan daku za'a fita yaƙin nan.." ta kalleshi da blue eyes ɗinta tace "kaima harda kai?.." ya nuna Angel yace "tare zamu tafi da Angel ranar monday, tinda daman can ne gurin aikinta.." Rumana kamar zatayi kuka tace "za'ayi asarar rayuka fa sosai, nayi weak da yawa..." Angel ce ta tsomo baki tareda faɗin "dajin da kika sani a baya toh yanzu babu wannan tsafukan, babu aljanu a cikin ta, saidai bamu san ƙarfin ikon da yakeda shi ba.." sake ƙiran wayar Rumana akayi a karo na biyu azabure ta tashi tana faɗin "sun sake ƙirana, bari naje na shirya.." da gudu ta nufi room ɗinta tana zuwa ta tuttusa kayanta a cikin akwatinta ta rufe da sauri ta fito tana jan akwatin, haka ta faɗo falo kamar daga sama ko canza kayan jikinta batayi ba, gajeren wandon nan ne ajikinta mai kakin soja sai baƙar t-shirt, ta saka takalmin ciki irin na sojoji ta fito tana musu sallama.. Mommy da Junaid da kuma Angel nufowa gurinta sukayi da sauri, mommy tana cewa "toh ki tsaya mana, wani irin gaggawa ne haka.." Rumana girgiza kai take tana cewa "mom sun bani time ne, sunce nan da awa biyu suke son ganina a Australian Headquarters..." tana kaiwa karshen maganarta ta rungumi mommy tana mata bankwana, ta juyo ta rungumi Angel tareda sumbatarta a kunci, ta nufi dinning table ta rungumo Ayush itama ta manna mata kiss a gefen fuska, taje yanda Aditi take itama ta rungumeta tareda mata kiss a kuncin ta, tukun ta tafo ta rungumi Junaid sosai tana kuka, shima rungumarta yayi sosai yana rarrashin ta, daga bisani suka rabe da juna, Junaid ɗaukar mata akwati yayi suka fita a tare domin shi zai kaita airport da motarsa... Aditi kam sumar zaune tayi jin za'a fita yaƙar sarki zalimu, tasan dole suma harda sojojin ƴan ƙasarsu kuma harda ita za'a sako, a matuƙar tsorace take domin shekarar data wuce sojojinsu sun kai farmaki can dajin amma ba soja ɗaya daya fito da rai, tana cikin wannan tunanin saiga hawaye zurzur asaman fuskar Aditi, daga yanzu itama zata fara tsammanin ƙiran waya daga wajen aikinsu na ƙasar china.... *WANNAN PAGE ƊIN NA SADAUKAR DASHI A WAƊANDA SUKE MUN COMMENT* *NAGODE MUKU SOSAI DA ƘARFAFA MUN GWIWA WARAN YIN TYPING, COMMENT ƊINKU YANA MATUƘAR NISHAƊARTAR DANI, INA SONKU SOSAI....* 𝑡𝑦𝑝𝑖𝑛𝑔✍️ 𝗠𝗔𝗧𝗔𝗥 𝗗𝗔𝗠𝗨𝗦𝗔 the wife of a tiger🐅🐅🐅🐅 𝙼𝚊𝚕𝚕𝚊𝚔𝚒𝚗 𝙰𝚜𝚖𝚎𝚎𝚝𝚊𝚑 ✍️✍️ 𝙿𝚊𝚒𝚍 𝚋𝚘𝚘𝚔 𝚌𝚊𝚕𝚕 𝚘𝚛 𝚠𝚑𝚊𝚝𝚜𝙰𝚙𝚙 09065443871 *💫💫{{N W A}}💫💫* Book two C̶h̶a̶p̶t̶e̶r̶ 11 ➡️ 12 washe garin ranar saturday da safe Mommy da Angel da kuma Ayush suna zaune a falo suna kallon film a Arewa 24, ita Ayush tana kallon ne amma tunaninta yana can gurin iyayenta, Aditi tana ɗakinta a kwance itama gaba ɗaya ta suƙure jin farmakin da za'akai ƙasar california tasan babu wanda zai rayu haka taketa tunanin nan, shima Junaid yana ɗakinsa a kwance idonsa a rufe kamar mai yin bacci amma kuma ba baccin yake yi ba, ƙarar message yaji ya shugo wayarsa ta whatsApp, hannu yakai saman drower yana lalumen wayar! ɗauka yayi sannan ya buɗe secuirity wayar yahau whatsApp, baƙuwar number ya gani an turo video, yana lumshe ido kamar mai jin bacci ya buɗe saƙon ya shiga kan videon abunda ya ganine yasa ya buɗe idonsa sosai a zabure ya tashi zaune zuciyarsa tana ɗarɗar, da ƙarfi ya furta "whatttt?..." wani irin bugu zuciyarsa tayi, "Yushert kuma? with bad boy? kuma acikin gidan nan hakan ma akan gadonta?..." zuciyarsa ce take tafarfasa ya sauƙa daga kan gadonsa a fusace yabar ɗakinsa, da sauri sauri ya sauƙa down stairs bai bi takan su Mommy ba haka yaje gaban Ayush yasa hannu ya fincikota ya wurgar da ita ƙasin carpet yana huci yace "daman ashe ke ba mutumiyar kirki bace? ke ƴar iska ce karuwa?.." Su mommy ne suka miƙe tsaye da sauri suna faɗin "lafiya kuwa?.." ɗaga musu hannu yayi yace "please mom karki dakatar dani" ya nuna Angel da yatsa yana faɗin "ke kuma karki kuskura ki saka mun baki..." ya kalli gurin da Ayush take a zaune a ƙasin carpet yace "Allah ya rufa mun asiri da ba'ayi baikon nan ba, wallahi da kin cuce ni saboda ni ba abunda nafi tsana arayuwata irin a munafurce ni, tirr da halinki, bazan taɓa Auran karuwa ba irin ki kuma munafuka..." Mommy ganin abun yayi tsanani ta dakawa Junaid tsawa tana faɗin "ya isa haka Junaid wani irin abune haka, kazo kana faɗan munanan kalamai akan yarinyar da bata san komai ba, yarinya mai haƙuri da juriya..." mommy bata ƙarisa maganar ba Junaid ya katseta da cewa "Mom duk abunda kike tunani ba haka bane, wannan yarinyar shaiɗaniya ce ƙazama karuwa...." bai gama iddasa maganar ba Mommy ta zabga masa mari har sau biyu tana kuka tace "nace ka dakata haka ko, shin ka sanar mun meyake faruwa ne? kodai ka haukace ne?..." cikin ɓacin rai yace "mom ba hauka nake ba amma zan nuna miki a zahiri..." ya miƙa mata wayarsa tareda faɗin "gashi nan ki kalla" hannun mommy na kakkarwa ta karɓi wayar ta danna kan video, ta soma kalla da hawaye caɓa caɓa a fuska, itama Angel ido ta kai kan video ta zaro ido sosai, Ayush tana daga zaune ta tashi da sauri taje itama tana kallon video, hannu tasa ta rufe bakinta tana kuka, Mommy da Angel gaba ɗaya juyowa sukayi suna kallon Ayush sun kasa cewa komai, murya na rawa Ayush tace "wallahi tallahi bansan da wannan videon ba.." Junaid wani irin kallo ya watsa mata yace "daman taya zaki san da wannan videon bayan asirinki ya tonu..." "wallahi Yaya Junaid bani bacee..." kafin ta rufe baki ya kai mata wani irin gigitaccen mari har saida ta faɗi ta kifu akan glass table dake tsakiyan ɗakin, nan take lips ɗinta ya fashe jini ne yake zuba sosai, juyowa tayi still bakinta bai rufu ba tana faɗin "wallahi ko zaka kashe ni bani bace, wallahi mai kama dani ne..." nan ma wani irin harbi yakai mata da ƙafarsa saida ta yi rigingine, yasa hannu ya zaro belt ɗin wandonsa zai kai mata duka, mommy tayi saurin riƙe shi tana faɗin "kana da hankali kuwa Junaid? ciwo zaka ji mata ne, ka tsaya kayi bincike akai tukun ka yanke hukunci...." fizgar hannunsa yayi da ƙarfi yana faɗin "mom wani irin bincike zanyi, bayan itace kuma da saninta tinda har magana take tana shashshafa shi balle kice ko tana bacci ne ko suma, kema kinsan wannan videon ba ƙarya bane, saboda taga babu kowa agidan shine zata kawo gardi cikin gidan nan?..." agigice Ayush ta tashi da gudu zata haura upstairs, yayi sauri yasa ƙafarsa ya girbe mata sawayenta saida tayi sama tukun ta faɗo akan stairs goshinta ne ya bugu har saida ya fashe, Angel ce ta taho tasha gabansa tana faɗin "wai meye hakane Junaid..." ɗauketa yayi da wani gigitaccen mari itama ta faɗa saman kujera, Mommy tsabar takaici ganin ciwonta zai iya tashi tayi saurin wuce wa ɗakinta ta danna sakata, Ayush kuwa kafin Junaid ya waiwayo kanta har ta miƙe da gudun gaske tayi hanyar waje tabar falon, gudu bana wasa ba haka ta nufi hanyar gate, shima Junaid ɗin bin bayanta yayi ya nufi hanyar gate yana magana da maigadi cikin ɗaga murya yace "Baba tsoho idan ka kuskura ka buɗe mata gate ayau zaka bar gidan nan..." maigadi jin abunda Junaid ya faɗa yasa kwaɗo ya kulle gate ɗin kafin Ayush ta iso, itama Angel fitowa tayi tana faɗin "Ayush karki tsaya ki gudu, ki wabci key ɗin a hannun maigadin ki buɗe kije ki ɓoye..." Junaid tsaya wa yayi har saida Angel ta zo zata wuce shi ta nufi gurin Ayush ya yi mata wani irin riƙo ya zazzabga mata mari sannan ya girbe mata sawu ta doku a ƙasi yana faɗin "ta gudu ko?.." tace "dan Allah kayi haƙuri Ogah Junaid...." kafin ta rufe bakin suka jiyo Baba maigadi ya ƙwalla ƙiran "yallaɓai Junaiddd..." waiwaya wa yayi yaga Ayush ce ta kama kunnensa ta garzaya masa cizo! da sauri ya miƙa mata key ɗin... ta tusa key ɗin a jikin ƙwaɗon cikin sa'a kuwa kwaɗon ya buɗu dasauri tasa hannu zata buɗe ta fice har ya iso yanda take ya cabki hannunta ya fara janta zasu koma ciki, tana ihu tana neman agaji ta kafa haƙwaranta akan damtsensa shima ta garsaya masa cizo, tsayawa yayi yana mata wani irin kallo ko motsawa bayayi, ita kuwa sai cizonsa take amma kamar mai cizon bishiya, kai wa hannu yayi ya zabga mata mari ta bayan hannunsa, agigice ta faɗi ƙasi tana ihu, tana shirin tashi ta gudu ya cabki wuyanta ta baya, tsabar a ruɗe take haka ta juyo takai bakinta saitin penus ɗinsa ta gasa masa cizo! ƙara yayi kaɗan ya durƙusa tareda riƙe gurin, ƙansa a ƙasin floor ya yi sujjada, shi kaɗai yasan raɗaɗin da yake ji a gurin, ya juma kansa a ƙasi bai ɗago ba, lokacin kuwa Ayush harta koma falo ta haura upstairs tana shiga ɗakinta ta danna sakata... itama Angel ganin yanda Junaid yayi tasan idan ya ɗago bazaiyi da wasa ba, haka ta tashi itama da gudu ta koma falo ɗakinta ta nufa tareda saka sakata itama... Maigadi ne ya yo kan Junaid yana faɗin "yallaɓai Junaid! yallaɓai Junaid!!! lafiya kuwa, kaima cizonka tayi ko?..." kafin ya iso dab da shi Junaid yayi saurin ɗaga masa hannu yana masa nuni akan ya tafi, still kansa a ƙasi bai ɗago ba... haka maigadi ya juya ya koma gurin aikinsa yana faɗin "yarinya saikace mayya, bansani ba kota gutsire mun kunne..." ya ƙarasa maganar yana shafa kunnensa.... ☆☆☆☆☆ Ɓangaren Sarki Ramoud! misalin ƙarfe 12 nadare Sarki Ramoud da Uma Bara'at suna kwance sunata faman shan baccinsu, kamar a mafarki Sarki Ramud yake jin kukan mujiyoyi da yawansu acikin masarautarsa, sai kuma yake jin wani irin dariya mai rikitarwa na ban tsoro, a gigice ya tashi yana waige-waige tareda jero addu'o'i a tunaninsa mafarki yake ashe duk ba haka bane, kallon yanda Bara'at take a kwance yayi yaga sai fama shan baccinta take, a hankali ya sauƙo daga kan gadon ya buɗe ɗakin ya fita, kai tsaye babban falon masarauta ya nufa, yana zuwa yaga wani irin haske mai kashe ido, hannu yasa yana tare idonsa da ganin wannan hasken, murya a disashe yace "waye anan? mekuma ya kawo ka cikin masarauta ta? meke tafe dakai?...." sassauta ƙarfin hasken akayi, hakan ya bawa Sarki Ramud daman ganin ko waye ne, ganin mutumin dake kan kujerar mulki yasa sarki zabura, zuciyarsa ne ya fara bugu da ƙarfi a hankali ya furta "MUNAFURR..." tintsirewa da dariya yayi jin sarki ya ambaci sunansa yace "na dawoo, daman ai nace zan dawo ko, to na dawo karɓar mulkin california a hannuna, kuma na dawo tareda ƙarfin ikona sama da wanda nake dashi a baya, babu mai iya dakatar dani ko waye ne..." Sarki Ramoud yace "meyasa kake son karɓar mulkin nan bayan bakada alaƙa da masarautar?..." Munafurr ƙara tintsirewa yayi da dariya tareda faɗin "yarjejeniyar da mukayi da kai har ka manta? to idan ka manta zan ƙara tunatar dakai, a shekarun baya kace na temaka maka waran mallakar manya-manyan aljanu domin su baka kariya, na kuma yi sanadiyar haɗaka da shuwagabannin aljanun ruwa da duk wasu aljanu suka amince maka da sharaɗin bazasu ga hawayenka ba har abada, ni kuma kayi mun alƙawarin indai aljanun nan suka ga hawayenka toh daga ranar zaka mallaka mun masarautarka shin ka tuno?..." Sarki Ramoud durƙusawa yayi da gwiwowinsa yana tsiyayar da hawaye a cikin ƙwayar idanuwansa sai a yanzu yake ƙarayin nadama akan kuskuren daya aikata a baya, ba tareda ya furta komai ba yaji anyi magana kamar daga sama, ana cewa "BABU WANDA YA ISA YA MALLAKI MASARAUTAR NAN INDAI BA WANDA YAKE DA ALAƘA DA ITA BA..." murmushin farin ciki Sarki Ramoud yayi ganin NARASIMHA ya bayyano, Munafurr shima miƙewa yayi tsaye yana faɗin "masarautar nan ya zamo nawaaa, babu wanda ya isa ya dakatar dani akan abunda nasa a gaba na..." cikin tsawa yake maganar tareda zaro takobinsa mai farfatsin wuta duk jikinsa yayi jawur, Narasimha kallon yanda Sarki Ramoud yake yayi tareda faɗin "wancan takobin da ka baiwa ɗiyarka shine makaryin tsafin wannan mummunan mutumin da zarar ya sareshi ko ɗan kaɗan ne, ka ɗauka ka baiwa Mayushert meye amfanin hakan? ga lokacin amfani da ita yazo..." Sarki Ramud ne yace "ka temaka Narasimha an ɗauko takobin nan.." Narasimha yana shirin ɓacewa zai je gurinsu Ayush domin ɗaukowa wannan takobin, Munafurr ya saita shi da takobinsa na tsafi saiga wani jar wuta kamar walƙiya ya fita daga jikin takobin ya shige ƙirjin Narasimha, lokaci guda Narasimha ya nemi hasken tsafinsa dazai ɓace ya rasa, an riga da an karya wannan tsafin Narasimha domin haske da wuta basa taɓa haɗuwa... inda ace Narasimha yayi saurin wurga masa hasken tsafinsa to da sihirin Munafurr ne zai karye amma Munafurr ya rigada ya aika nashi saƙon zuwa ƙirjin Narasimha, Narasimha ganin yanzu bashida wani sihiri hakan yasa ya amar da wani zobe daga cikin bakinsa ya wurga wa Sarki Ramoud yana faɗin "Raamoud ga wannan zoben kayi saurin sanya shi a yatsarka saika murza ka ɓace kaje ka ɗauko wannan takobin a ɗakin sirrin Junaidu, zoben zai kaika har yanda takobin yake kayi saurin kawowa ko kai da kanka zaka iya fitar masa da jini da wannan takobin shikenam shima nashi yazo ƙarshe... kamar yanda Narasimha ya sanar masa haka kuwa yayi yana shirin ɓacewa Munafurr zaiyo kansa da gudu, Narasimha yayo tsalle ya doku akan Munafurr duk suka baje a ƙasi, sarki Ramud kuwa har ya ɓace, Macizen da suke jikin Munafurr ne suke kai wa Narasimha sara, ga dafi ne dasu kamar bala'i, Munafur ne ya ɗago sannan ya buɗe bakinsa saiga macizai da yawansu suna fito wa, masu jajayen kamannu, sunada kayuwa bibbiyu, haka suka shishshige cikin gashin jikin Narasimha, shi kuwa miƙewa yayi yanata faman wurgar dasu, duk da saran da suka masa amma yaƙi kwanciya, haka idanuwansa suka canza launin jaa sosai, gashin jikinsa sunyi birtsi-birtsi sun tashi tsaye, Macizai kuwa sunfi ɗari biyar a jikinsa manya da ƙananu duk suna mammanne a jikinsa, Munafurr ganin Narasimha yaƙi kwanciya haka ya ɗaga takobinsa mai farfatsin wuta ya fille kan Narasimha dashi, cikin ƙanƙanin lokaci saiga kayin Narasimha a ƙasi ya faɗo, amma duk da hakan gangan jikin Narasimha yana a tsaye yaƙi faɗuwa, macizai kuwa duk sun harhaɗe masa ƙafafuwa da ko ina na jikinsa... wani irin dariya Munafurr yake yi ya koma kan kujerar mulkin ya zauna tareda jingina bayansa a jikin kujerar ya ɗaura sahu ɗaya akan ɗaya yanata tintsirewa da wani irin mahaukacin dariya, jin kururuwar dariyar yasa Bara'at fitowa falon cikin gaga'ar bacci take faɗin "wai meke faruwa ne?..." saida ta fito tsakiyar falon tukun taci arba da Narasimha tsaye tsangamgam ba kayi sai wuya, murtsike idonta tayi tana son tabbatar wa ko mafarki take, ganin gangan jikinsa ne a tsaye babu kayinsa ga kuma yanda macizai suke zarya a jikinsa, idonta ta kai saitin kayinsa dake wurge a gefe, ido ta zaro waje da sauri takai idonta kan Munafurr dake zaune akan kujerar sarauta, baki ta buɗe zatayi ihu, ya hura mata wani hayaƙi daga cikin bakinsa lokaci guda kuwa bakinta ya rufu sannan idanuwanta suka daina gani sai duhu kawai, ga ido a buɗe amma bata iya ganin komai, muryar ta kuma ya shaƙe babu halin magana ta zama kurmiya... Damusa kuwa tin zuwan Munafurr ya nemi wani ɗan lungu ya ɓoye a gurin ko motsinsa ba'a ji, Damusan yana da hankali domin yasan indai suka haɗa ido da Munafurr to bazai barshi ba, shi kuma Munafurr a tunaninsa Damusa ya daɗe da mutuwa tin lokacin da ya wurga masa maciji a jiki... Sarki Ramoud kuma sauƙa yayi a ɗakin Junaid yana ɓuɓɓuya saboda kar ya haɗu da Junaid, gani yayi babu kowa a cikin bedroom ɗinsa, yayi tunanin ko yana cikin toilet haka yake sanɗa zai wuce cikin ɗakin sirrinsa, hannu yasa ya tura ɗan ƙofar da zai shige, cikin sa'a kuwa ƙofar ta buɗu, cikin muryar tsawa Sarki Ramud yaji ance "waye ne awaran nan?..." Junaid ne a cikin ɗakin yana ta faman daddanna computersa tin daga lokacin da yaji zasu fita yaƙar sarki Ramud daga lokacin yake ta faman neman mafitar yanda zasuyi su je farmakar sa, ba bacci kullum acikin abu ɗaya yake, Junaid ne ya taso a fusace ya fito cikin bedroom ɗinsa ganin babu kowa yasa yayi tsuka tareda faɗin "sarki zalimu! sarki Raamud wannan karan ba kuliya zaka turo mun ba, ba aljanu zaka turo mun ba ko kai da kanka zaka zo mun awannan lokacin kwananka ya kusan ƙarewa, domin ina daf da kawo maka farmaki".... yakai idonsa kan agogon bangon ɗakin yaga ƙarfe 2 nadare, kansa gaɗi ya nufi hanyar fita ya buɗe ɗakinsa ya fice, shi kuwa Sarki Ramud daman ɓoyewa yayi ata gefen wardrobe yana jin duk abunda Junaid yake faɗi, girgiza kai kawai yayi ya shige cikin ɗakin nan, zoben hannunsa ne yake nuna masa yanda takobin yake ta hanyar bada haske, har yazo zai wuce yaga photon masarautarsa a cikin computer Junaid, tsayawa yayi yana kallon girman fadarsa a cikin computer jin motsin mutum yana shirin shugowa, ƙirjinsa yayi wani irin bugawa ga hasken da zobensa yake badawa alamun suna daf da gurin takobin kenam... Junaid ne ya shugo hannunsa riƙe da ruwan Faro, shi kuwa sarki RAMUD har ya ɗauki takobin ya murza zoben ya yi ɓacewarsa, saiga Sarki Ramud acikin babban falon masarauta, ganin a yanda Narasimha yake yasa ya rikice yana faɗin "Narasimhaaa! NArasimhaa!! Narasimhaaa!!! ya nufi gurin da yake da gudun gaske bai san lokacin da yayi wurgi da takobin hannunsa bama, takobin tsalle yayi ya faɗa cikin wani lungu sai a gaban Damusan da yake ɓoye a gurin, ko shi Munafurr bai lura da yanda takobin ta faɗa ba.. Sarki Ramud yana shirin rungumar Narasimha kawai yaci karo da macizai suna ta zarya a gangan jikinsa, kafin kace mai macijen nan sun faɗar da gangan jikin Narasimha ƙasi ga yanda sukayi fata-fata da jikinsa duk sun fiffige gashin jikinsa, zuciyar sarki Ramud ne ya hauro cikin ɓacin rai ya kurma ihu tareda nufan yanda Munafurr yake a zaune zai kai masa duka, Munafur riƙo ƙafar sarki Ramud yayi ya ɗago shi sama da hannu ɗaya yasa hannu biyu ya ɓalla ƙafar sarki Ramoud gida biyu kamar wanda ya ɓalla ice ya wurgar dashi gefe guda gurin da Bara'at take a zaune ba gani ba ji ba magana haka take zaune bata san a wani hali ake ciki ba, sarki Ramud ƙafarsa ya riƙe yana ta kururuwar ihu ga ƙafa yanata lanjal-lanjal kamar zai tsinke tsabar an raba ƙashin ƙafar gida biyu...... Munafurr tashi yayi ya d'auko wani qaton kwalba Mai marfi ya d'auki kan Narasimha ya Saka aciki sannan ya rufe kwalbar, 'kiran wata 'katotuwar mujiya yayi tazo ya d'aura mata gangan jikin Narasimha ya bata umarnin taje ta jefashi cikin kogin ruwan da ba'a ganin 'karshenta.... ya nemi guri ya cigaba da zamansa akan kujerar masarautar ya d'auki hular sarautar Sarki Raamud ya sanya a kansa... *TAB AKWAI YAƘI FAH, DOMIN YAƘIN SOJOJIN NAN ZAI IYA KOMAWA KAN MUNAFURR...* *AUNTY ADITI GWARA FA KIYI KUKAN DA GASKE DOMIN INA TUNANIN SOJOJIN NAN HMMMMM, KUDAI FARA KUKA TIN DAGA YANZU AHAMMMM NIDAI BAKINA DA GOROO..* *TOH READERS SHIN WANNAN PAGE ƊIN NAKU NE KO NAWA?...* 𝑡𝑦𝑝𝑖𝑛𝑔✍️ 𝗠𝗔𝗧𝗔𝗥 𝗗𝗔𝗠𝗨𝗦𝗔 the wife of a tiger🐅🐅🐅🐅 𝙼𝚊𝚕𝚕𝚊𝚔𝚒𝚗 𝙰𝚜𝚖𝚎𝚎𝚝𝚊𝚑 ✍️✍️ 𝙿𝚊𝚒𝚍 𝚋𝚘𝚘𝚔 𝚌𝚊𝚕𝚕 𝚘𝚛 𝚠𝚑𝚊𝚝𝚜𝙰𝚙𝚙 09065443871 *💫💫{{N W A}}💫💫* Book two C̶h̶a̶p̶t̶e̶r̶ 13 ➡️ 14 Ɓangaren su Junaid... washe garin ranar sunday da safe Ayush tana kwance asaman gadonta, sai faman juye-juye take kwata-kwata a daren jiya ko rintsawa batayi ba, tana ta tunanin yanda akayi ta kusanci wani ba tareda sanin ta ba, acikin ranta take faɗin "tayaya hakan zata faru? yaushe hakan ya faru dani? bazan taɓa yadda da wannan video cewa nine ba" tana cikin wannan tunanin taji ana knocking ƙofar ɗakinta, sai da ta ɗan juma kafin tazo zata buɗe domin kafin ta tashi ma aiki ne tsabar yanda jikinta ke mata ciwo ga wani irin zazzaɓin da take, kafin ta buɗe saida ta tambaya "waye ne?.." murya ciki-ciki domin daƙer yake fitowa... "Angel ce ki buɗe.." daga waje ne aka bada amsa, Ayush buɗe mata ɗakin tayi sannan ta juya waran da gadonta yake ta zauna a bakin gadon, itama Angen shugowa tayi tareda rufe ɗakin tazo ta zauna kusa da Ayush tana kwallonta cikin tausayawa, gashi yanda goshinta ya fashe gurin yayi jawur, lips ɗinta ma ya ɗan kumbura kaɗan, idanuwanta duk sunyi jawur tsabar kukan da ta sha, ga ta kwana batayi bacci ba.. bayan Angel ta ƙareta da kallo ta sauƙe ajiyar zuciya tana faɗin "Ayush bai kamata kisa wani abu aranki ba, nasan kina cikin damuwa sosai amma ki rinƙa danne wa, zaman kaɗaicin nan da kikeyi a cikin ɗaki shi kaɗai ma zai jawo miki ciwo, Hmmm! na fahimci har yanzu baki gama sanin ko waye Junaid ba, shi ba irin mazan nan da za'a rinƙa nuna musu damuwa bane domin shi bai damu da ganin mutum acikin damuwa ba, kina ganin mommy gata can a ɗaki tana fushi da shi amma tin jiya baije ya dubata ba, cizonsa da kikayi bayan ya gama mutsul-mutsul sa haka ya tashi ya shige room ɗinsa nin tin daga lokacin ban ƙara ganinsa ba, duk da nima fece wa nayi cikin ɗakina amma ina kallonsa ta window" bayan ta kai ƙarshe shuru ta ɗanyi tana kallon gefe guda daga bisani ta ɗago tana kallon Ayush ta kuma cewa "Ayush amma taya aka samu video nan? shin da gaske ne ko kuma ƙage ne don a ɓata miki suna?..." Ayush da sauri ta juyo tana kallon Angel har idonta ya cicciko tace "wallahi tallahi Aunty Angel bansan da wannan video ba, wallahi ni bansan mutumin bama.." Angel tace "toh amma ai acikin room ɗinki aka aikata hakan.." Ayush cikin yanayin kuka take magana "wallahi bansani ba, ni bana fita waje, kuma bani da waya a hannuna ban ma iya waya bama kwata-kwata balle na ƙira mutum cikin ɗaki na..." Angel cike da mamaki tace "to amma taya hakan zai faru? bincike ya nuna alokacin da duk aka tafi asibiti ne hakan ya faru, amma kuma abun zai ban mamaki...." Ayush kuka ne ya kuɓuce mata sosai take yin kukan, Angel shuru tayi kamar mai tunanin wani abu a zabure tace "ina buƙatar ƙara ganin video nan domin tabbatar da wani abu, in har da gaske kece kika aikata hakan da saninki zan gani, in kuma duk shiri ne nan ma zan gani, bayan ni soja ce haka kuma ni ƴar C.I.D ce mai bincike nice mai warware ƙullin da aka daɗe da ƙullawa, ko a wajen aikin mu ne duk abunda ya gagara ni ake nema domin na warware komai saboda haka ki kwantar da hankalinki insha Allahu zan magance matsalar kinji ko.." ta ƙarasa maganar tareda bubbugar kafaɗar Ayush wacce taketa sheshsheƙar kuka, Angel fice wa tayi daga ɗakin ta nufi ɗakin Junaid tsayawa tayi tana knocking a hankali, zuciyarta tana ɗarɗar gudun kar har yanzu bai saƙƙo ba, tana cikin wannan tunanin taji har an buɗe ƙofar, Junaid ne ya tsaya yana kallonta fuskar nan a ɗaure ba annuri yace "ya akayi?.." bin ta gefensa tayi ta shige ciki tana faɗin "toh ka shugo mana..." ɗan tsuka yaja sannan ya rufe ɗakin shima ya shugo ya nemi guri ya zauna yana kallon gefe, itama Angel ɗin zama tayi a gefensa tana faɗin "Ogah Junaid wai har yanzu baka huce bane?..." shuru yayi mata bai ce komai ba, ta kuma cewa "nazo ne akan batun case na video nan da aka turo maka.." tsuka yaja sannan ya juyo yana kallonta da lufu-lufun idanuwansa da suke buƙatar bacci yace "meyasa kike son shiga abunda bai shafeki ba ne, so what's your problem about this robish thing..." jan dogon numfashi tayi sannan tace "i want to close the case..." dogon tsuka yayi ya juyo yana kallonta yace "mind your own personal business please Angel, wannan case ɗin bai shafeki ba, meyasa kike son wahalar da kanki akan abunda gashi nan a aikace ya faru da gaske, toh ma mezaki bincika?...." murmushi Angel tayi sannan tace "ina son ganin wayanka" yace "me zakiyi da ita?.." murmusawa tayi sannan tace "i want to show you something..." "which something?.." in short answer ya bata yana kallonta, tace "please Ogah Junaid i beg you.." ɗaukar wayan yayi ya miƙa mata, da sauri ta kai hannu ta karɓa, kai tsaye whatsApp ɗinsa ta hau ta shiga kan number da aka turo saƙon, ta ɗauki number a wayanta tayi dialing call ji tayi number a kashe... murmushi Junaid yayi tareda kawar da kansa gefe yace "hauka suke zasu bar layinsu a on.." itama Angel murmushi tayi sannan tace "abun na munafurci ne shiyasa an turo ne domin a warware soyayya..." Junaid yace "an turo dai domin a temake ni kuma ko da ba'a turo bama na rigada na yanke hukuncin rabuwa da ita saboda babu macen da zata rinƙa juyani kamar ɗanta.." Angel tace "bazaka gane bane Ogah Junaid, shin babu wanda kake zargi a wannan al'amarin?.." "kinga Angel banida lokacin sauraron tambayoyinkin nan, kin saka ni agaba kamar wata ƴar jarida kina mun tambayoyi shin nufin ki na amsa miki ne? you are mad! stand and get out inside my room, i don't what this robish..." ya miƙe tsaye ya kuma cewa "give my phone" yana kaiwa hannunsa zai karɓa, Angel a zabure ta riƙe hannun Junaid tana faɗin "laaa ogah Junaid kalli wani abu acikin video nan.." jawo hannunsa tayi ta zaunar dashi tana nuna masa video tareda faɗin "ka kalli video nan dakyau Ayush ba'a cikin hayyacinta take ba.." yayi tsuka tareda kallon gefe yace "daman taya zata zauna cikin hayyacin ta bayan tana rungumai da gardi.." tace "ba haka bane wanda yake musu video yana kusa dasu, kuma da duk kan alamun akwai munafurci aciki, Ayushart tana da matuƙar jin kunya, inda ace da sanin ta wallahi bazata bari a ɗauki video ba, amma zan cigaba da bincike na..." suna cikin wannan halin sai suka jiyo bugun ƙofa, Junaid ne yayi maganar yace "yes come in" turo ƙofar akayi a hankali, da mamaki a fuskar su suke kallon Aditi wacce take a silent jikinta duk ya mutu ga hawaye caɓa-caɓa a fuskarta, da sauri Junaid ya miƙe ya nufi gurin da ta tsaya yana faɗin "Aditi what is wrong with you? why are you crying?.." hannu tasa ta rungume shi tana kuka, shima rungumarta yayi yana rarrashinta, daga baya ya ɗago da fuskarta suna fuskartar juna yace "took to me mana Aditi.." tana kuka tace "nima an ƙirani agurin aikin mu wai na koma china a yau akwai yaƙi a gaban mu, kuma nasan a yaƙin nan babu wanda zai dawo da ransa..." ajiyar zuciya ya sauƙe tareda cewa "ki kwantar da hankalinki Adity, insha Allahu zamu ci nasara akan yaƙin nan, babu wanda zai mutu kinji ko.." ɗaga masa kai tayi sannan tace "to ni yanzu zan wuce airp inason jirgin da zai tashi da wuri, akwati na yana falo already nayi sallama da mommy itama tana jirana a falo.." hannu yasa yana goge mata hawayen fuskarta yace "muje mu to na kaiki filin jirgin..." juyawa sukayi suka fice daga cikin room ɗin a tare, sai iya Angel kawai suka bari a zaune a bakin gado, Aditi kuwa ko lura da ita batayi ba tsabar idonta a rufe suke damuwar ta shine yaƙin da zasu fita... bayan sun sauƙa downstair Aditi ƙara rungumar mommy tayi suka sake yin sallama, Junaid yace "mom zan rakata....." mommy tayi saurin ɗaga masa hannu tareda cewa "kar ka mun magana Junaid..." yace "toh..." ya riƙe hannun Aditi suka fita yana jan akwatin kayan ta.. ☆☆☆☆☆ ata ɓangaren su Doctor Hasheem kuma yana zaune a falo ne shi da Lailah suna kallon plasman, Lailah har yanzu haushin Aditi take yi dukan da tayi mata, amma ta wani ɓangaren ta sauƙo zuciyar ta wasarr take tura video da tayi wa Junaid, ita kaɗai sai murmushi take tayi tana tunanin awani hali Ayush take ciki ne domin tasan halin ogah Junaid saiya ɗauki ƙwaƙƙwaran hukunci akanta... tana cikin wannan tunanin taji Doctor Hasheem yana cewa "ni Lailah kin kaiwa Maimoon abinci kuwa?.." a zabure ta miƙe tana faɗin "wallahi na manta bros bari nakai mata..." ta nufi kitchen ta ɗauko flask ɗin abinci da flask ɗin ruwan shayi ta miƙi hanyar da zai kaita ɗakin da maimoon take.. Maimoon tana zaune akan katifa taji motsin mutum yana tafowa da sauri ta miƙe tsaye ta laɓe a bakin ƙofa, daman ta ƙudurta a ranta cewa yau kam zata bar gidan nan, zata koma gida tinda yanzu ta samu sauƙi tafiyarta ya koma normal, ɗaukar ƙwalba tayi acikin ranta tace "wallahi ko waye rausa masa zanyi akai domin ba mai dakatar dani akan hanyar tafiyata.." Lailah ce tasa key ta buɗe ƙofar da kayan abinci a hannunta ta shugo, tana shugowa kuwa Maimoon ta ɗaga ƙwalbar nan ta kwaɗa mata a goshi, wani irin ƙara Lailah tayi, tasau kayan abincin a ƙasi ta dafe goshin nan ta faɗi a ƙasi sumammiya, haka Maimoon ta tsallake ta da gudu tayi hanyar fita adaiden lokacin saiga Doctor Hasheem ya tafo jin ihun Lailah, ƙoƙarin tare Maimoon yake yana faɗin "ina zakije kuma?.." ƙure mata gudu yayi ya riƙo kunkumin ta ya ɗagata saman kafaɗarsa, ihu take tana kururuwa ganin yana shirin komar da ita cikin ɗakin yasa ta kafa bakinta a saitin wuyansa ta gasa masa cizo, ai kuwa ba shiri ya sauƙe ta ƙasi, yana sauƙeta ta zage tayi masa wani ƙwaƙƙwaran bugu a saitin penus ɗinsa da gwiwowinta, durƙusawa yayi yana ihu.. a lokacin ta samu damar fece wa har saida ta isa bakin gate ta buɗe tana fita kuwa saiga mai keke napep tayi saurin hawa suka miƙi bakin hanya.... ☆☆☆☆☆ Ɓangaren Sarki Raamud.. yana zaune yana jimamin mutuwar Narasimha ga kuma nakasa shi da akayi, shi sai a wannan lokacin ya fahimci matarsa bata gani sannan bata ji, azabure ya riƙo ta yana girgiza ta tareda ambatar sunanta "BB! BB!! BB!!! meya faru dake dan Allah kiyi mun magana mana.." ita kuwa babu bakin magana sai hawaye, Munafurr yana zaune akan kujerar sarauta yaji sarki Raamud duk ya rikirkice yana ta ƙiran sunan matarsa, tintsirewa yayi da dariya tareda faɗin "taurin kan ka ne ya jawo nayi muku hukunci daidai daku, kai na raba ƙafafunka biyu, ita kuma matarka na makantar da ita sannan na kurmantar da ita, shi kuma wanda kuka ɗauke shi a matsayin abun kariya na gama da rayuwarsa, na raba kansa da gangar jikinsa...." ya sake tintsirewa da dariyaa... Sarki Raamud ne ya ɗaga hannayensa biyu ya haɗe su guri guda yana hawaye yace "Munafurr da roƙeka ka tausaya mun ka sassauta hukuncin ka akan matata domin ita bata san komai ba, ni na yadda kamun komai amma ka ƙyale matata..." Munafurr kallonsa yayi da jajayen idanuwansa sannan yace "ni banida niyar cutar dakai, amma ka nuna mun taurin kai ne, ka saɓa alƙawarin da muka ɗaukar..." Sarki Raamud yace "kayi haƙuri indai mulki ne na bar maka, na bar maka masarautar nan, amma ka warkar mun da matata.." ƙara tintsirewa da wani irin mahaukaciyar dariya Munafurr yayi sannan yace "yanzu naji magana Raamud, bama iya matarka zan warkar ba hatta kaima zan warkar da ƙafafuwanka amma bazaku fita daga cikin masarautar nan ba saboda kana fita kwananka ya ƙare domin mutanen garin jira suke ka fita su ɗau ranka, zaka zauna da matarka a cikin ɗakinku ban yarda ku leƙo nan falon masarautar ba, zan kafa nawa tarihin acikin wannan masarautar, zan kafa nawa manya-manyan Aljanu acikin wannan masarautar, zan ninka ka ƙarfin ikon da kake dashi a bayaa..." yana gama maganganunsa kuwa ya busar da hayaƙin bakinsa kan Bara'at, nan danan idanuwanta suka buɗu, bakinta ya buɗu, shima sarki Raamud ɗin an warkar da ƙafafunsa sun koma normal, Bara'at kallon sarki Raamud tayi tana kuka ta rungume shi sosai, shima rungumarta yayi yana rarrashinta... Munafurr ne ya darara musu tsawa tareda faɗin "ku tashi ku koma cikin ɗakin ku, matarka tanada ciki har ta haihu kar naga kowa acikin ku ya fito falon nan, domin zan zuba manya-manyan aljanu ne suyi mun gadi.... da sauri Sarki Raamud ya ɗauki BB suka nufi upstairs mai hawa uku nan ne ɗakinsu ... ☆☆☆☆☆ Mommy tana zaune a falo kan sofa saiga Angel ta sauƙo down sai faman kalle-kallen saman falon take kamar mai duba abu, Mommy tace "ke kuma fah Angel mai kike nema?.." tace "mom ina duba cameran falon nan ta ina yake.." mommy ta ɗaga yatsanta tace "gashi can.." Angel da sauri ta kalli gurin tana faɗin "yes good! good, yanzu komai zai zomun a daidai, zan duba shige da ficen mutanen da suka shugo, zanga wannan mummunan mutumin shi da wa suka shugo ɗakin nan..." Mommy tace "bangane mai kike nufi ba?.." Angel tace "mom akan matsalar video da akayi wa Ayush ne, inaso na kawo ƙarshen matsalar..." Mommy tace "kina tunanin ba ita bace?.." Angel tace "gaskiya ita ce amma bana tunanin a cikin hayyacin ta akayi mata haka, amma ko ma waye yasa akayi mata haka sai na gano shi kuma zan sa a kamo shi dumu=dumu..." Mommy tace "gaskiya nima abun ya ɗaure mun kai, har yanzu ban yadda cewa Ayushert zata iya aikata haka ba, to ma yarinyar da ba fita ko ina take ba balle tasan mutane aina zata samo mutumin nan? kuma ba wayane a hannunta ba, da iya Junaid kawai ta shaƙu, bata san kowa ba inba Junaid ba, ni ko cewa akayi tayi ciki wallahi zanyi tunanin Junaid ne yayi mata, amma abun yayi matuƙar ban mamaki.." dogon numfashi Angel taja sannan tace "Allah sarki tana zaune zuciyarta ɗaya amma tanada maƙiya a gefe, yanzu dai mom aina computer camerorin gidan nan yake? inaso zanje na duba..." Mommy tace "tab ai duk wasu abubuwan tsaro suna ɗakin Junaid, ɗakin ma can secret room kuma bazaki san da ɗaki a gurin ba, ki bari ya dawo saiki lallaɓashi kije ki duba duk da baya barin kowa ya shiga amma wata ƙil ke ya iya barinki tinda ga wayarsa ma a hannunki..." dariya Angel tayi sannan tace "haba dai nifa ƴar hannun damarsa ce pah, ƴar gaban goshinsa kuma ƴar amanarsa ai dole ma ya barni na shiga wannan ɗakin domin aiwatar da bincike na, tinda shi baya duba camerar tsaro bai san abunda ke wakana acikin gidan ba, shi wato yafi bada himma akan Sarki Raamud..." tana daga tsaye ta kama kunkumi ta ɗan turo bakinta sannan ta kuma cewa "naga Aditi uwar bala'i har da kukan ta ita a dole tana tsoron karta mutu, ashe duk bala'in ta tana tsoro? nipa Mom wallahi yaƙin nan da za'a fita ko a jikina domin bana jinsa a raina, kwata-kwata ban damu ba..." Mommy tsaya kallonta tayi tace "Hmmm! toh ke kuma uwar surutu kafin ki gama surutain nakin kije kitchen ki girka mana Indomie, domin yunwa nake ji, ga Ayush itama yanzu bata samu taci...." Angel wuce wa kitchen tayi tana cewa "kafin na kammala ai Oga Junaid zai dawo, sai yaje ya buɗe mun secret room ɗin...." 𝑡𝑦𝑝𝑖𝑛𝑔✍️ 𝗠𝗔𝗧𝗔𝗥 𝗗𝗔𝗠𝗨𝗦𝗔 the wife of a tiger🐅🐅🐅🐅 𝙼𝚊𝚕𝚕𝚊𝚔𝚒𝚗 𝙰𝚜𝚖𝚎𝚎𝚝𝚊𝚑 ✍️✍️ 𝙿𝚊𝚒𝚍 𝚋𝚘𝚘𝚔 𝚌𝚊𝚕𝚕 𝚘𝚛 𝚠𝚑𝚊𝚝𝚜𝙰𝚙𝚙 09065443871 *💫💫{{N W A}}💫💫* Book two C̶h̶a̶p̶t̶e̶r̶ 15 ➡️ 16 Ayush tana kwance abun duniya duk yabi ya isheta, kwatsam sai abu ya faɗo mata arai! a razane ta tashi tana faɗin "littafin tarihin mahaifina, yana ina? na shiga uku aina na ajiye shi, kar wani ya ɗauka, asiri na zai tonu wayyo.." dasauri ta tashi ta buɗe ɗakinta ta nufi ɗakin Junaid, cikin sa'a kuwa ta samu ɗakin a buɗe ta shige, bincike ta soma yi a ɗakin tana ɗarɗar kar yazo ya sameta, gaba ɗaya drowers ta bubbuɗe da wardrobe amma bata ga alamar littafin da takobin ba, zama tayi a bakin gadonsa tayi tagumi tana tunanin aina zata samu takobi da kuma littafin, hankalinta ne ya dawo jikinta ta ɗago tareda kai eyes ɗinta waran secret room, a ranta tace "wancan ɗakin na meye neh? me ake ajiye wa a gurin? tabbas indai Yaya Junaid yaga waɗannan abubuwan to bazasu wuce can ɗakin ba..." tashi tayi a hankali take tafiya har ta iso saitin ɗakin tasa hannu ta tura ko zai buɗu cikin rashin sa'a taji ɗakin a rufe ansa masa key, yarfe hannayenta biyu tayi cikin nuna damuwa tace "kashhh..." a ruɗe ta juyo ta nufi drowers tana checking key ɗin ɗakin, duk ta duba bata gani ba, har ta haƙura ta juya zata fice a ɗakin tayi tunanin ɗaga pillow bed ɗinsa, tana dubawa kuwa saiga key, a hanzarce ta ɗauka taje ta buɗe ɗakin, abunda ta fara gani shine ƙaton photon mahaifinta, shi ya ja hankalinta taje gaban photunan dake a mammanne a jikin bango ta tsaya, ganin photon mahaifiyarta kuma yasa ƙirjinta bugawa da ƙarfin gaske, kafin kace wani abu hawaye duk ya wanke mata fuska, tana kallonsu tana zubda hawaye ita har ta manta abunda tazo dubawa, tana cikin wannan halin taji motsin mutum ta wajen ɗakin wato bedroom, gabanta ne ya yanke tana faɗin "innalillahi wa inna'ilahi raju'un, nashiga uku ya dawo..." Bayan shugowar Junaid cikin ɗakinsa zama yayi a bakin gado ya dafe kayinsa da hannayensa biyu yana kallon ƙasi kamar mai tunanin wani abu, yana cikin wannan halin yaji an turo ƙofa an shugo, ɗaga kansa yayi ya kalli Angel ya maida kansa a yanda yake tareda faɗin "jarababbiya kin dawo kenan.." Zama tayi daf dashi tace "my man daman kai nake jira ka dawo, akwai wata alfarmar da nake so kayi mun.." Ɗagowa yayi yana kallonta yace "ina jinki..." tace "daman! daman!! daman so nake na duba cameran tsaro na gidan.." yamutsa fuska yayi yace "mezaki duba?..." cikin shagwaɓa take magana tace "inason duba fice da shige na mutane a ranar shagalinka.." Ba tareda ya kalleta ba yace "akwai abunda ya faru ne agidan?.." Kamar zata yi kuka tana yarfe hannu tace "kaiii Ogah Junaid I can't answering your questions is too much.." juyowa yayi yana kallonta cikin yanayin jin bacci yace "ok leave my room if not.." tana turo baki tace "toh daman akan case ɗin Ayush ce..." girgiza kai yayi sannan yace "daga ke har ita banida lokacin ku.." Da sauri ta durƙusa ƙasi ta ɗora hannayenta biyu akan cinyarsa tace "Please My man I beg you ka temaka mun na gano gaskiyar lamarin, dan Allah ita fah Ayush ko baka ɗauketa a matsayin budurwa ba ya kamata ka riƙeta a matsayin ƙanwarka ita fah marainiya ce batada kowa in baku ba, nasan dai bazaka bar ƙanwarka ta shiga cikin wannan matsalar kuma ka shareta ba...." Dogon numfashi yayi sannan yace "maganarki gaskiya ne but Yushert tayi hurting heart ɗina da yawa, koda yaushe matsala take kawo mun, idan har bazata iya faranta mun ba nima kuwa bazata ga abunda take so daga wajena ba, especially video da aka turo mun nayi danasanin haɗuwa da yarinyar nan, naji bana ƙaunarta a raina, wallahi na tsaneta bana sonta tinda har zata iya aikata wannan ƙazantar da ƙazamin mutum irin wannan ɗan shaye-shaye haba tirr, Angel idan zakiyi maganar Yushert kada ki sake sakoni acikin wannan al'amarin, na riga da na yanke alaƙata da ita, kije kiyi binciken ki amma babu ruwana..." Angel kanta a sunkuye kamar ta rausa ihu tsabar takaicin jin kalaman Junaid daƙer take motsa baki tace "shikenam insha Allahu bazan sake yi maka maganar Ayush ba, yanzun ina key ɗin ɗakin?.." Ayush tana daga cikin secret room tana jin duk tattaunawar da suke yi akanta, sam bata jin daɗin furucin Junaid ba haka take kuka a hankali mai cin rai, jin Angel ta tambayi ko key ɗin ɗakin da take ciki yasa ta zabura ta samu bayan kujerar ɗakin ta ɓuya a gurin!.... Idon Junaid ne yayi jawur tsabar baƙin cikin da yake ji idan ya tuno da video Ayush, kamar ya fashe da kuka haka yake ji, a hankali ya furta "ki duba ƙasi pillow zaki ga key..." Da sauri Angel ta tashi ta nufin gurin ta ɗaɗɗaga pilolin bata ga key ba tace "My man nifa Banga key ba..." Ɗago da kansa yayi da sauri yana kallon gurin, tunani ya shiga yi shifa a saninsa da hannunsa ya ajiye key ɗin nan, sai a lokacin ya fara bin ɗakin da kallo yana jinjina kai yace "da duk kan alamu an shugo mun ɗaki kuma anyi mun bincike.." ya kai idonsa gurin da ƙofar ɗakin secret room yake ya tashi yana takawa a hankali yaje gurin, hannu yasa ya turo ƙofar sai yaga ta buɗu, zaro ido yayi waje da ƙarfi ya furta "whattt..." ya juyo bayansa yana kallon Angel yace "kin shugo mun ɗakin nan before?.." Girgiza kai tayi tace. "wallahi ban shugo ba, girki nayi wa mommy..." kafin ta ƙarisa maganar ya katseta da cewa "bana son ƙarya fa da kuma munafurci..." murya na kakkarwa Angel tace "wallahi tallahi Ogah Junaid ka yadda dani ban taɓa yi maka ƙarya ba, ban shugo bedroom ɗin nan ba sai yanzu..." Girgiza kai yayi sannan yace "good...." ya shige cikin ɗakin yana kalle-kalle, Ita kuwa Ayush tana bayan kujera tayi shuru ko motsi baka ji,. saida ya gama dudduba babu kowa yana tsaye idonsa suka sauƙa akan jan material ɗinta akwai ɗan zirin da bai gama ɓuya ba, Junaid tsayawa yayi yana murmushin gefen baki irin na muguntan nan, ya ɗauki pillow kujera ya jefa mata shi, a tsorace ta tashi tana kuka a zabure tayo kan Junaid tana faɗin "ganan kuliyar kwanaki tazo zata cutar dakai Yaya Junaid, ta rungumeshi sosai! hannu yasa ya finciketa tareda wurgata saman kujera yana zazzaro ido yace "meya kawoki cikin room ɗin nan? me kika zo yi? sannan ki gaya mun taya kika san akwai ɗaki anan?..." tasowa tayi tana faɗin "dan Allah Yaya Junaid kayi haƙuri, ka daina jin haushi na, wallahi ban aikata abunda kake zargin na aikata ba...." Junaid zuciyarsa ce ta hauro sosai ga takaicin bata amsa masa tambayarsa ba, cikin zafin nama ya cabki wuyanta ya gwara da jikin bangon ɗakin, ƙara ɗaya tayi ta sume a gurin tsabar bugun da yayiwa kayinta, zata faɗi ƙasi yayi saurin riƙeta ya mannata a saman ƙirjinsa ya ƙanƙameta sosai shima fashewa yayi da kuka, Hajijiya ne yake shirin ɗaukarsa yana rungume da Ayush ya zauna daƙer akan kujera, ita kuma ko motsi batayi ido a rufe sai goshinta da yaketa ambaliyar jini, shima duk ya ɓata jikinsa da jinin da Ayush take zubarwa, ya kwantar da kansa akan sumar kayinta yana ta faman zubda ƙwallah.... Angel tana zaune a bedroom taji shurun yayi yawa har zuwa wannan lokacin Junaid bai fito daga cikin wannan ɗakin ba, miƙewa tayi ta nufi ɗakin don ganin meke faruwa domin duk ihun da za'ayi a cikin ɗakin nan ba jiyo mutum za'ayi ba sakamakon ta cikin ɗakin akwai glass door, shige cikin ɗakin tayi taga ta ko ina haske ne tana juya ɓangaren damanta taga Ogah Junaid yana zaune ya kifa kansa a tsakiyar kayin Ayush, ga kuma jini duk ya ɓata masa kayan jikinsa daman kayan milk ne, Da sauri ta ƙariso gabansa tana faɗin "My man lafiya kuwa meya faru da Ayush? taya ta shugo ɗakin nan? amma kuma jini yana zuba mata fah sosai yakamata aje ayi saurin tsayar mata...." Ɗagowa Junaid yayi ya zame mata ɗan ƙaramin gyalenta wanda ta ɗan ɗaure gashinta dashi, ya ruɓanya gyalen biyu sannan ya ɗaure mata goshinta, yana kammalawa yabi doguwar kujerar ya kwanta ya kwantar da Ayush a samansa yana kallon sama ita kuma fuskarta yana kife asaman ƙirjinsa har wannan lokacin tana nan a sume... Angel tsayawa tayi tana kallon ikon Allah tace "Ogah Junaid...." Kafin ta furta wani abu taji ya katseta da cewa "Please bana jin daɗin jikina ga can computer ki duba abunda kike son dubawa" tace "toh shikenam" ta nufi gurin tana maganar zuci "oh Junaid da Ayush ikon Allah, wato duk wanda yace zai shiga tsakaninku ma shi zaiji kunya, toh yanzun me yayi wa Ayush ne? ita kuma Ayush metazo yi nan cikin ɗakin bayan tasan baya barin kowa ya shugo saida sanyewarsa..." haka taketa tunanin nan har ta zauna akan chair tasa computer agaba tana ta faman daddannawa, can kusan awa guda Angel tana duba lamarin nan kuma ta gano domin tana zargin da sa hannun mutane biyu.. A ruɗe ta juyo tana kallon yanda Junaid yake a kwance ido a lumshe ko motsi baya yi tace "Ogah Junaid na binciko komai wallahi wannan video da aka turo maka ba gaskiya bane, domin bayan Ayush ta bar gurin taron baikon ku kai tsaye ɗakinta ta nufa, bayan wasu mintuna kuma saiga wannan matar mai liƙab wanda babu san ko ita wacece ba ta shiga ɗakin Ayush, daga baya kuma bayan wasu mintuna na shiga ɗakin Ayush amma saidai matar nan bata fito ba, amma kuma ban sameta a cikin ɗakin Ayush ba toh amma abun ya ɗaure mun kai kenam jin shugowata matar ta ɓuya kenam? to ni bayan na fito matar bata fito ba har waran awa 3 lokacin kenam muna asibiti, Laylah ta shiga ɗakin bata fito ba sai bayan wasu mintuna kuma sai ga wannan mutumin shima ya shiga ciki, Ni abun yayi mungun ɗaure mun kai! mutane uku ne suke cikin ɗakin Ayush toh idan hakane Ayush batada masaniya akan abunda ya faru da ita, mata biyu acikin ɗakin namiji ɗaya sunyi amfani da wannan namiji ne domin su ɓata mata suna, amma kuma daga baya namijin ne ya fara fitowa sai kuma Lailah ta fito itama, gashi camerar kuma ta nuna da mangariba Ayush ta fito sanye da dogon hijab ɗinta ta fice a lokacin hospital ta nufa nasani domin a wannan lokacin taje asibiti, to kuma ina matar nan mai liƙab najira fitowarta amma shuru har yanzu har kuma yau duk shige da fice da ake yi bata fito ba, to kodai Aljana ce?...." Bayan ta gama surutanta ta kuma cewa "Ogah Junaid kaji fah yanda ake ciki.." taji shuru bai bata amsa ba still ta sake ƙiran sunansa "Ogah Junaid! Ogah Junaid!! My Man lafiya kuwa kodai bacci ne ya ɗauke ku..." ta tashi taje gurin da suke a ƙwance tana bubbugar kafaɗarsa tareda ƙiran sunansa amma ko motsi babu itama Ayush ko motsi, tasa hannunta a saitin hancinsu basa numfashi a ruɗe Angel ta miƙe tsaye tana faɗin "innalillahi me kuma ya faru, nashiga uku mommy.." ta fice a ɗakin da gudu tana ƙwalla ƙiran mommy.... Ogah Junaid shima numfashin sa ne ya ɗage cak a sume yake... ********* Maimoon ce take zaune a kan gadon Ammynta sai faman rera kuka take, Mahaifiyarta ta sakata a gaba tanata mata tambayoyi acikin damuwa, "Maimoon magana nake miki kin kasa bani amsa shin ina kika je tsawon kwanakin nan? baki taɓa tafiya wani waje ba tareda kin sanar mun ba, kuma baki taɓa yin wannan kwanaki a wani waje ba Maimoon so kike ki jawo mana abun magana?..." Girgiza kai Maimoon kawai tayi ta kasa cewa komai, suna cikin wannan halin saiga mahaifinta ya shugo shima yace wa Ammy "ta gaya miki yanda taje ta?..." Ammy tace "a'ah tin jiya naketa binta akan ta sanar mun amma taƙi..." Daddy yace "Okay.." ya fice a gigice, ba jumawa ya shugo hannunsa riƙe da wayar wuta yana zuwa ya fara zabga mata ajiki, Maimoon ihu take tana kuka tanata sose-sosai har saida ya faffasa mata jiki abunka da farar mace, dakatawa yayi da dukanta yana zazzaro mata eyes yace "zaki faɗa mun yanda kika je ko kuma na cigaba da dukanki?..." tana kuka tace "wallahi Daddy nima bansan yanda nake ba, wasu mutane ne suka kama ni suka ajiyeni awaransu, bana fita ko ina yanzun ma guduwa nayi basu sani ba..." Daddynta yace "su waye ai dai kinsansu, kuma miye alaƙar ki dasu?.." tana shessheƙar kuka tace "nima ban sansu ba, ina cikin tafiya taji an sakani a mota daga nan na nemi hankalina narasa..." Daddy a fusace yace "ƙarya kike kice anyi kidnapped ɗinki domin da sun nemi kuɗi a waran mu..." Ammy ta taso itama tana kuka tsabar tausayin ɗiyarta tazo gaban Daddy tace "Abul Bintu ka dubi wannan al'amarin Maimoon bata taɓa wannan dogon zango ba kuma ba tareda sanin mu ba, kaima dai kasan munada maƙiya zasuyi hakane domin su ƙuntata maka, fatan mu tinda Allah ya kuɓuto mana da ita mugode wa Allah kawai, amma ni na yadda da ɗiyata ɗari bisa ɗari..." Dogon numfashi Daddy yaja idonsa akan Maimoon wacce kanta ke sunkuye yace "su nawa ne mutanen? kuma zaki iya gane fuskokinsu? sannan akwai abunda sukayi miki ne?..." Maimoon ɗagowa tayi tana faɗin "gaskiya Daddy bazan iya ganesu ba saboda koda yaushe da baƙin hula a fuskokinsu, sun kai su goma amma babu abunda sukayi mun kawai dai acikin wani ɗan ɗaki suka kulle ni.." Daddy ya kuma cewa "zaki iya gane gidan da suka kai ki?.." Dasauri ta girgiza kai tace "a'a bansan lokacin da aka kaini gidan ba kuma lokacin dana fito ban tsaya dubawa ba saboda ina tsoron kar su fito su kamani..." Daddy goya hannayensa yayi ta saman ƙirjinsa yace "inason shugo da hukuma cikin wannan al'amarin su binciko mun su waye ne waɗannan mutanen..." Ammy tace "a'a Abul Bintu kar ka fara domin wannan maganar ba kowane ya sani ba, idan aka shugo da hukuma ai kowa zai san da maganar kuma akwai masu zargi da yawa, nidai a shawarce mu bar maganar nan a iya cikin gidan nan, ƴata da mutuncinta a idon jama'a kuma mahaddaciyar alƙur'ani, bazaiyu azo ana mata mummunar fassara ba..." Daddy yace "toh shikenam tinda kince haka..." yayi ficewarsa acikin ɗakin, Da gudu Maimoon ta tashi ta rungumi Ammy tana kuka mai cin rai... Duk tattaunawar da sukayi kuwa Laylah tazo ta laɓe musu taji duk maganganun da sukayi tin daga lokacin da aka fara dukan Maimoon, jin fitowar Daddy ne yasa tayi gudu ta koma falo ta zauna, Daddy yana fitowa Laylah ta durƙusa har ƙasi ta gaishe shi ya amsa mata tareda cewa "ki tashi kice gurinsu suna cikin ɗaki, kinzo ganin ƙawarki ko.." ya ƙarisa maganar yana murmushin yaƙe domin bayaso ta fahimci wani abu... Itama tashi tayi tana dariya ta shige ciki, tana shiga kuwa ta samesu suna zaune asaman gado Maimoon ta ɗora kayinta akan cinyar Ammy. Da sallama Laylah ta shiga, Ammy ta amsa mata cikin nuna damuwa, Samun guri Laylah tayi ta zauna suka gaisa da Ammy ta juyo tana kallon Maimoon tace "ashe Besty nah ta dawo.." Ammy tace "wallahi kuwa Laylah wai ashe gidan kawunta taje ta toh sai matarsa ta riƙeta! sunyi ta ƙiran wayata basu samu ba, kuma yanzu basu da number Daddyn ta, dake ba'a Nigeria suke ba suna ƙasar Iran..." Laylah tace "too har ƙasar Iran taje ta kuma bata sanar ba?.." Ammy tace "cewa tayi baƙin cikin yayanki Hasheem ne yasa ta yanke hukuncin barin Nigeria, yanzun nan Daddynta ya gama yimata faɗa ai, ta tsoritar damu sosai wallahi..." Laylah ta jinjina kai suna kallon kallo itada Maimoon tace "gaskiya Besty baki kyauta mana ba, kin hana mu bacci kullum acikin tunaninki muke..." Wani irin harara Maimoon ta wurga mata ta juyar da kansa gefe guda.. Ammy tace "Maimoon baki ga Aminiyarki tazo bane?..." 𝑡𝑦𝑝𝑖𝑛𝑔✍️ 𝗠𝗔𝗧𝗔𝗥 𝗗𝗔𝗠𝗨𝗦𝗔 the wife of a tiger🐅🐅🐅🐅 𝙼𝚊𝚕𝚕𝚊𝚔𝚒𝚗 𝙰𝚜𝚖𝚎𝚎𝚝𝚊𝚑 ✍️✍️ 𝙿𝚊𝚒𝚍 𝚋𝚘𝚘𝚔 𝚌𝚊𝚕𝚕 𝚘𝚛 𝚠𝚑𝚊𝚝𝚜𝙰𝚙𝚙 09065443871 *💫💫{{N W A}}💫💫* Book two C̶h̶a̶p̶t̶e̶r̶ 17 ➡️ 18 Mommy ta shugo ɗakin Junaid da gudu kamar wacce zata kifu, Angel na biye da ita a baya haka suka shugo har secret room a yanda Angel ta barsu ahaka ta dawo ta tarar dasu, Mommy jawo Ayush tayi daga saman Junaid zata faɗi ƙasi sukayi saurin tareta su biyu suka haɗu suka ɗauki Ayush sukayi ɗakinta da ita suna shiga suka kwantar da ita akan gadonta tace "kInsan wani abu Angel ke zaki zauna da Ayusher ki yayyafa mata ruwa, ni kuma zanje naji da Junaid, Angel tace "toh shikenam Mom..." dasauri ta nufi toilet zata ɗebo ruwa, ita kuwa mommy har ta fice, da sauri ta shiga ɗakin Junaid ta samoshi a ɗayan room ɗin da bottle a hannunta na ruwan sanyi, tana zuwa ta fara watsa masa ruwan akan face ɗinsa, a hankali yake buɗe eyes ɗinsa ba tareda ya firgita ba! dishi-dishi yake kallon ceilling, ya ƙara lumshe idonsa tareda sauƙe numfashi, Mommy ce ta ɗaga kansa tukun ta zauna tareda kwantar da kansa kan cinyarta tana faɗin "Babana kana lafiya?..." buɗe eyes ɗinsa yayi yana motsa bakinsa a hankali ya furta "Mom my heart zai fashe.." ya riƙo hannun mommy ya ajiye asaitin zuciyarsa.. Mommy tace "My son ka kwantar da hankalinka ba abunda zai samu zuciyarka, ka daina saka abu a ranka kaji ko Babana..." ya ɗago ƙwayar idonsa yana kallon Mommy yace "mom kin daina fushi dani?.." Momy tace "daman ba fushi nake dakai ba, kaine idan ranka ya ɓaci baka iya control kanka, yanzu meye amfanin dukan Ayush? banaso ka mayar mun da yarinya jaka, yanzu ma naga naji rauni akan goshinta kuma nasan kaine! shiyasa take tsoron Aurenka ai...". ta sauƙe numfashi tareda kallon gefe tana shafar sumar kayinsa, yana kallon ceilling yace "tayi mun laifi babba Mom, meyasa zata kwanta da wani namiji daban wanda bani ba? bazan iya juran haka ba..." Shuru Mommy tayi bata ce masa komai ba... Ayush ce take zaune asaman gadonta sai faman rera kuka take bayan Angel ta farfaɗo da ita, hakuri Angel take bata tana rarrashinta tareda cewa "Ayush kema bakya jin magana wallahi, bayan kinsan a halin da ake ciki yanzu Junaid ba'a cikin nutsuwarsa yake ba, mai zai kaiki ɗakinsa har ma ki shiga yanda ba'a lamunce miki ba haba dan Allah, gashi yanzu kin jawo ya fasa miki goshi bayan baki gama warkewa da dukan da yayi miki ba..." Share hawayenta Ayush tayi sannan tace "kenam ni an mayarni dabba kullum acikin dukana ake, nifa ba yarinya bace! na mallaki hankalin kaina, saboda Yaya Junaid gaba ɗaya zaman gidan ya isheni, ni tafiya zanyi bazan iya rayuwa acikin wannan ƙuncin ba kullum ina cikin zubda hawaye, ina zaune a cikin gidan masu kuɗi amma ba kwanciyar hankali a cikin gidan kamar wacce nake cikin prison..." ta ƙarisa maganar tana kuka. Angel tace. "a'ah ki kwantar da hankalinki gobe ma Junaid zai bar Nigeria kuma kafin ya dawo komai zai daidaita, idan kikace zaki tafi Mommy bazataji daɗi ba..." Ayush jin gobe zasu tafi yaƙar iyayenta saita sake fashewa da wani sabon kukan, daƙer Angel take rarrashinta har Ayush ta ɗan kwanta bacci... daga nan Angel ta miƙe ta fice a ɗakin, da sauri ta sauƙa downstairs ta fice daga falon ma, tana zuwa gurin parking motocin gidan ta zaɓi ɗaya ta shiga tareda tayar da motar ta miƙi hanyar get, maigadi ne yayi saurin buɗe mata get ganin yanda ta tafo da gudun gaske, tana fita daga gidan ta miƙi hanyar gidansu Laylah.. Shi kuwa Junaid yana tsaye a bakin window ɗakinsa yana ganin lokacin da Angel ta fita masa da ƙaramin motarsa jeep, Mommy ta daɗe da barin room ɗinsa domin yanzu haka tana kitchen... Junaid komawa ɗayan room ɗinsa yayi yanason duba cameran tsaro na gidan shima, yana zaune ya kafa eyes ɗinsa akan computer, a cikin camera video daya gani ya fuskanci abubuwa da dama, jinjina kai ya shiga yi yana murmushi, tashi yayi ya koma bedroom ya ɗauko phone ɗinsa yazo ya jona a jikin computer zai kamo location na contact ɗin da aka turo da video ta WhatsApp bayan yayi tracking number, computer ta nuna number a nan garin Abuja take, yana bibiyar number har ta kaishi yanda layin take a ajiye wanda tazararsu da ɗan rata kaɗan,. daya bi location kuma sai computer ta nuna masa gidan Doctor Hasheem, ƙara jinjina kansa yayi yana zargin mutum biyu acikin gidan nan! Doctor Hasheem ko kuma Lailah, duk da baiga Doctor Hasheem ya shiga ɗakin Ayush ba amma yana konkonto akansa, kodai Doctor Hasheem ne yasa Lailah ta haɗa Ayush da gardin nan ko kuma Lailah ce tayi hakan saboda ta ɓata sunan Yushert, Amma kuma yana tunanin shin wacece matar nan mai liƙab.... yana cikin wannan tunanin wani abu ya faɗo masa arai dasauri ya shiga wani ɓoyayyen camera shutting na cikin ɗakin Ayush domin acikin ɗakinta ma yasa camera amma sai dai baya dubawa sakamakon ita kaɗai ce a ɗakin, kafin ya shiga camerar ɗakin Ayush saida yasa security wanda ba wanda zai iya ganewa sai iya shi kaɗai, yana duba video abunda ya faru a cikin ɗakin bayan Ayush ta shiga da gudu tana kuka saiga wannan matar mai liƙab yana son ganin fuskar matar saidai kash camerar bayanta ya ɗauka banda fuskarta, ga kuma lokacin da Ayush ta tafo zata rungumeta Umantata ta hankaɗata tareda marinta, sai abun ya ƙara ɗaurewa Junaid ƙwaƙwalwa, dasauri ya ɗauki abun jin magana ya kara a kunnuwansa yana jin duk tattaunawar da sukeyi, yaji Ayush tana ƙiran Uma kuma duk maganar da sukayi akan Junaid ne yaji Uma tana cewa "idan baki Auri Junaid ba, Babu ni ba ke kuma bazaki sake ganina ba har abada.." Junaid ƙwaƙwalwarsa ce ta fara juyawa yana faɗin "me hakan yake nufi? shin wacece wannan matar? daman Yushert tanada iyayenta a raye? kenam munafurtar mu take yi? shin meyasa ta ɓoye mana abubuwa da dama?..." abunda yake masa yawo kenam a ƙwaƙwalwarsa,. gani yayi matar ta shige toilet da gudu a yayinda Angel ta shugo, bayan ta fita kuma matar ta fito, a lokacin ne yake da damar kallon fuskar matar saboda ta fuskanci camera saidai kash tin a cikin toilet tasau liƙab ɗinta ta fice a ɗakin, amma saidai abunda ya ƙara ɗaure masa kai a camera waje baiga fitarta ba, yana zaune can saiga Lailah ta shugo ɗakin, duk yana kallonsu yana kuma sauraron abunda suke faɗa, gani yayi Lailah ta curo magani ta bawa Ayush daga nan kuma hankalinta ya ɓace mata, daga baya kuma saiga mutumin nan ya shugo, yana kallon yanda Lailah take musu video, Ran Junaid ne yayi matuƙar ɓaci sosai, ya dafe goshinsa tareda tusa tafin hannunsa cikin sumar kansa ido a rufe, shi kaɗai yasa irin raɗaɗin da yake ji aransa, Kawar da video waransu Lailah yayi yana son bibiyar matar data fita daga ɗakin Ayush kafin su Lailah su shugo domin matar tafi tsaya masa arai, camerar wajen ɗakin Ayush ya buɗe gani yayi matar ta tsaya a bakin ƙofar Ayush bayan wasu ɗan seconni yaga ta ɓace ɓatt A razane Junaid ya miƙe tsaye yana zaro ido waje yana ja da baya... ******** Angel ce ta shige cikin gidan su Lailah bayan maigadin gidan ya buɗe mata, saida yaje ya tambayo aka bashi umarnin ya buɗe mata, dasauri Angel ta fito daga cikin motar ta nufi hanyar mashigar shiga falon, Shiga tayi ta samesu sunata hira a falo ga plasman ana showing India film, Iya su kaɗai ne a falon daga Doctor Hasheem sai kuma Lailah, Lailah tana bashi labarin abunda ya faru a gidansu Maimoon data je suna dariya, Ganin Angel yasa duk suka miƙe tsaye suna kallonta saida Angel taje gabansu kafin tayi musu sallama tana murmushi! Lailah har da kuka ta tana faɗin "innalillahi Yayana sune suka mun duka a hospital Koh, yanzun ma sunzo su ƙara sumar dani wayyo Allah nasara.". tana ɓoye a bayan Doctor Hasheem. Dariya Angel tayi sannan tace "awww daman kinada tsoro Lailah? gaskiya ban taɓa tunanin kinada tsoro har haka ba, bani na dakeki ba kuma banzo gidanku don na dake ki ba amma kuma idan kika nuna mun rashin gaskiya akan abubuwan da zan tambayeki toh kuwa nima zan dakeki, duka ma irin wanda bakiyi zato ba...." ta ƙarisa maganar tana zaro mata ido. Doctor Hasheem ne yace "lafiya kuwa Malama ya za'ayi kinzo gidansu kuma kice zaki dake ta, ina ruwanta daku meyasa kuke son shiga rayuwarta ne, marainiyar Allah kodan kuna ganin ku sojoji ne shine kuke iya zalincin ku..." Angel ce ta ɗaga masa hannu tareda cewa "dakata Mallam Hasheem ba gurinka nazoni ba amma kuma za'ayi komai a gabanka! ku zauna domin ba wani ɓata lokaci zanyi ba..." Gaba ɗayansu zama sukayi, Angel tace "Lailah nazo gurinki ne saboda muna zargin wani abu daya faru, ki sani duk tambayoyin da zan miki karki sako mun ƙarya a ciki domin faɗar gaskiyarki shi zai sa ki kuɓuta daga zargin da ake miki..." Gaban Doctor Hasheem ne ya buga da ƙarfin gaske a zabure yace "Please meya faru?.." Angel ɗaga masa hannu tayi ta dakatar dashi tareda cewa "koma meye ne ai zaka ji.." Doctor Hasheem shi tunaninsa kar maganar akan Maimoon ce, Ita kuma Lailah tintinin tasha ruwan jikinta domin ta saddaƙar akan video Ayush ne, zuciyar ta kuwa sai bugawa yake da ƙarfi-ƙarfi... gyara zama Angel tayi sannan tace "Lailah a ranar shagalin Ogah Junaid da misalin ƙarfe 5 meya kaiki ɗakin Ayush?.." Duk da fankan da yake kaɗawa a ɗakin amma haka Lailah take ta sharar gumi tana muzurai bakinta na motsi mutsil-mutsil, Angel ce ta katseta da cewa "magana nake miki Lailah, ko ba amsa?.." Dasauri Lailah ta ɗago tana ƙiƙƙina tace "wallahi tallahi ba abunda ya kaini ɗakin Ayusher, kawai dai mun samu matsala ne shine aranar naje neman yafiyarta kuma ta yafe mun..." Angel tace "toh meye kike ta faman wallewa shin kinsan abunda ke faruwa ne? abunda na tambaye ki kenam fah amma dubi yanda kika rikice mun, kina ɗakin Ayush akwai wanda ya shiga ɗakin shin wayene?.." Lailah tana zazzarowa ido waje tace "ehhh to ina zaune da Ayush akwai wanda ya shugo shine nake tambayarta ko wayene wannan tace mun baƙonta ne, daga nan na tashi na barsu a ɗakin..." Jinjina kai Angel tayi sannan tace "Lailah bana son ƙarya! nagaya miki idan kika mun ƙarya babu ke babu fita daga cikin wannan case har a gano gaskiyar, idan kuma Junaid yasan kina cikin wannan Case toh kiyi kuka da kanki, zaki raina mun wayo naga kusan awanku guda a cikin ɗakin Ayush, mutumin yana ciki kuma kusan a jere kuka fito daga ɗakin shine farkon fitowa before ke.." Lailah fashewa tayi da kuka tana faɗin "wallahi tallahi fitowa nayi na shiga ɗakin Ogah Junaid nayi bacci..." Angel hannu tasa a aljihun wandonta mai kakin soja ta ciro bindiga tace "ƙarya kike Lailah ɗakin Ogah Junaid da hannuna na kulle da key kuma lokacin key ɗin ɗakinsa na hannuna, shin zaki gaya mun gaskiya ko saina ragargaza miki ƙafa ki zama gurguwa..." A ruɗe Lailah take faɗin "a'ah dan Allah ki rufamun asiri karki harbeni ƴar uwa zan gaya miki, Wallahi! Wallahi!! Wallahi!!! ki temakeni fitowa nayi na tsaya a bakin ƙofa ina jiran su, amma ni bana cikin ɗakin.." Angel tace "kenam iya su biyu kika bari a ɗakin?.." A gigice Lailah tace "eh eh ehh wallahi..." Jinjina kai Angel tayi tana murmushi tace "toh amma waye ya musu video?.." Lailah tace "nima ban saniba.." Kunna kunamar bindigarta Angel tayi ta saita ƙafar Lailah tace "ina dai baki saniba?.." Ihu Lailah ta fara kurmawa a gidan tana magiya, Shima Doctor Hasheem ɗin tasowa yayi da sauri yana roƙon Angel yace "kiyi haƙuri mana Angel kibi komai a hankali kar tsautsayi yasa ki harbeta.." Angel juyowa tayi tana kallon Doctor Hasheem cike da takaici tace "whattt! tsautsayi fah kace Hasheem, ni ai bansan tsautsayi ba, abunda yake raina kawai nake aikatawa, domin mu harbi ba komai bane a gurin mu! bazan harbeta a wajen da zata mutu ba amma idan bata gaya mun gaskiya ba zan harbeta agurin da zata jikkata, Doctor Hasheem kaje ka zauna inajin kunyarka fah, banaso ka shiga lissafin da ba naka ba..." komawa Doctor Hasheem yayi ya zauna domin yasa Angel wani sa'in batada Annuri idan Alluran sojan ta ya motsa... Durƙusawa ƙasi Lailah tayi tana kuka tareda faɗin "dan girman Allah kiyi mun rai Aunty Angela wallahi banida laifi bansan komai ba, kuma bansan wanda ya tura video baaa.." ta ƙarasa maganar tana kuka. tsawa Angel ta darara mata tace "kiyi mun shuru, ai Lailah kin ƙara jefa kanki cikin masifa indai baki gaya mun gaskiya ba, taya kika san an tura video?..." Shuru Lailah tayi bata ma san ta faɗin hakan ba, ƙiƙƙina ta soma yi maganar ta na rawa ba'a jin abunda take faɗa ma, tsabar rikicewar da tayi.. A fusace Angel ta tashi taje har gabanta ta zabga mata wani irin gigitaccen mari tace "ki buɗe baki kiyi mun magana ko kuma na tafi dake headquarters su Ogah Junaid yanzun nan..." Girgiza mata kai Lailah ta shiga yi tace "nine na tura video.." Angel tace"ke ko? to meyasa kika tura? sannan wannan gayen da kuka haɗa baki dashi yazo kuka tozarta Ayush wayene shi?..." Lailah tace "a'ah wallahi a ɓoye nayi musu basu sani ba, sunyi tunanin na tafi nikuma ɓuya nayi nayi musu, kuma na tura video ne saboda na ceci rayuwar Ogah Junaid domin Ayusher karuwa ce ƴar iska, tana bin yawon hotel..." Kafin ta ƙarasa maganar Angel ta ƙara zabga mata mari tace "kiyi mun magana cikin ɗa'a, sannan a ɗaukar video nan bai nuna alamar a ɓoye akayi shi ba, a saitin gadon mai ɗaukar yake tsaye yake video..." Shuru Lailah tayi bata ce komai ba, tana tunanin mai zatace ne.. Angel tace "kinyi shuru Lailah ko dai kina jiran sauƙar wani marin?.." A tsorace Lailah ta ɗago tana cewa "wallahi sune sukace na ɗauke su a video sai a turawa Ogah Junaid saboda Ayush bata son Aurensa, wai ita da wanda take so..." Angel tace "ita Ayush ce tace ki ɗauketa a video?.." Lailah tayi saurin ɗaga kanta tace "Ehhh..." Angel tace "toh ita ɗin Ayush wa tace takeso?.." Da sauri Lailah ta nuna Doctor Hasheem tace "Yayana wai take so..." Angel girgiza kai tayi tana dariya tace "toh ita kuma mata mai liƙab fah?.." Lailah tace "wata mata mai liƙab?..." Angel ce ta danƙwaleta tace "kin ci ubanki, matar da kuka shiga kuka sameta a ɗakin Ayush fah?..." Lailah ta ɗora hannayenta biyu akayi ta tace "nashiga uku wai meyasa ake son jefani cikin matsala ne, wallahi tallahi wuta bal-bal idan kika tuhumeni akan wata mata kumadu domin banganta ba wallahi ban sameta a ɗakin Ayush ba..." Angel zaro ido tayi waje tace "Lailah ni ce wuta balbal? bani number mutumin da kika haɗashi da Ayushert munafuka kawai..." Lailah tace "wallahi banida number saa.." Kafin ta ƙarisa maganar Angel ta darara mata tsawa tace "ki bani number sa nace miki..." A tsorace Lailah ta ɗauki wayarta ta lalumo number mutumin ta bawa Angel.. Angel tace "ki tabbatar ba wrong number kika bani ba.." Lailah cikin kuka tace "wallahi tallahi numbersa ne..." Angel ta karɓi wayar ta ɗauki number mutumin sannan tayi tracking wayar Lailah saboda duk wayar da tayi zata sani, in ma ta ƙira mutumin ne akan ya gudu Angel zata sani, domin Aikinta ne acikin aikin soja wato yin bincike, da kuma warware matsala, Yanzu Lailah ta shugo hannu tinda har akayi tracking ɗin wayarta... Tashi Angel tayi ta miƙa mata wayarta tace "kinji kunya wallahi Lailah, kin kasa haƙura da Junaid shi kuwa ba ke bace a gabansa ba, kina yarinya ƙarama amma kin iya munafurci, duka duka bazaki wuce shekara 18 ba a duniya amma kin iya salon munafurci, Allah ya temakeki bana zaman Nigeria yanzu dana koya miki hankali wawiya kawai..." Daga nan Angel tayi tafiyar ta... Bayan fitar Angel da mintuna 30 Lailah ta ɗauki wayarta ta gudu cikin ɗakinta, Shi kuwa Doctor Hasheem shuru yayi yana kallonta domin ya gano ko meke faruwa... Lailah tana shiga ɗakinta ta danna ƙiran number mutumin da ake ƙira da sauro, Itama Angel tana tuƙi acikin motar taji wayarta tana ring-ging dubawa tayi taga Lailah ce take ƙiran wayar mutumin da ta karɓi numbersa, Murmushi Angel tayi tareda girgiza kai! Bugu ɗaya kuwa mutumin ya ɗauki ƙiran Lailah, Angel ta danna recording sannan tasa a speaker ganan muryar Lailah raɗau a wayar Angel tana faɗin "Hello Sauro ka samu ka cire sim card ɗinka domin ana bincike akan video danayi muku kai da Ayush wacce Ogah Junaid yake son Aura.." Cikin Muryar gardawa Sauro yace "kinga abunda nake gaya miki koh? daman nace miki wannan aikin bazan iya yinsa ba saboda bana shiri da a'halin sojoji domin riƙonsu ba kyau, kika sakani dole gashi yanzu kin sakani a cikin matsala.." Lailah tace "toh naga na baka kuɗin aikinka, nidai yanzu kam ka gudu, shin kana inane?.." Sauro yace "toh naji amma kafin na sanar miki yanda nake shin soja ta karɓi wayarki?.." Lailah tace "eh mana ta ɗauki number ka" Sauro yace "tirrr ƙaramar ƴar boko baki saniba ko tayi tracking wayarki, Ina wannan layin da kika tura video toh ki ƙirani dashi saina gaya miki..." tace "toh shikenam.." tana ƙatse ƙiran ta ɗauko ɗayan sim card ta ɗaura ta ƙira Sauro... Wannan wayan kam kaf Angel taji duk tattaunawar su, murmushi kawai tayi amma saidai taso taji a yanda mutumin yake... Ƙiran da Lailah tayi da ɗayan number shima Junaid yayi ƙirƙiransa ta yanda zaiji duk wayanda akayi da number ta computer, yana zaune kuwa yaji ƙira ya shugo computer sa saida ya jira wanda aka ƙira ya ɗauka tukun Junaid shima ya danna record ya sanya abun sauraro a kunnensa yaji duk wayar da suka ƙarisa yinsa tsakanin Lailah da kuma Sauro, Junaid jinjina kai yayi sannan yace "Lailah! Lailah!! Lailah!!! zaki shugo hannu na..." Shi abunda ya ƙara rikirkitashi shine ɓacewar wannan matar da Ayush take ƙira da Uma, yana maganar zuci yace "kenam Yushert Aljana ce? daman da Aljana muke zaune? nima abun zai ban mamaki taya za'ace batada zuriya ko ɗaya..?" Ɗaukar wayarsa yayi ya danna ƙiran wayar Angel bugu ɗaya ta ɗauka tareda cewa "Hello My Man..." Yace "kina ina?.." tace "yanzu zan shawo kwanar layin unguwar mu.." Yace mata "toh ki juya baya yanzun nan Lailah ta ƙira wanda yayi video da Yushert zai tafi airport yace Ghana zai tafi a yau, but ki nemi wasu sojoji a headquarters Kamar guda biyu ko uku kuje tare..." Tace "toh shikenam yanzu kuwa thanks for help..." katse wayar yayi yana sauƙe numfashi, ya kwantar da kansa a jikin kujerar da yake zaune ido a lumshe kamar maiyin bacci..... Ita kuwa Lailah duk wayar da tayi Doctor Hasheem yana laɓe a bakin ƙofa yaji duk wayar da tayi... *DAN ALLAH BAKWA COMMENT BEFI MUTANE UKU BANE MASU COMMENT, KUMA YAWAN COMMENT ƊINKU SHI ZAI ƘARFAFA MUN GWIWA WARAN TURO MUKU UPDATE AKAI AKAI....* 🙏🙏🙏🙏🙏🙏🙏 𝑡𝑦𝑝𝑖𝑛𝑔✍️ 𝗠𝗔𝗧𝗔𝗥 𝗗𝗔𝗠𝗨𝗦𝗔 the wife of a tiger🐅🐅🐅🐅 𝙼𝚊𝚕𝚕𝚊𝚔𝚒𝚗 𝙰𝚜𝚖𝚎𝚎𝚝𝚊𝚑 ✍️✍️ 𝙿𝚊𝚒𝚍 𝚋𝚘𝚘𝚔 𝚌𝚊𝚕𝚕 𝚘𝚛 𝚠𝚑𝚊𝚝𝚜𝙰𝚙𝚙 09065443871 *💫💫{{N W A}}💫💫* Book two C̶h̶a̶p̶t̶e̶r̶ 19 ➡️ 20 Sauro yana tafiya sauri-sauri gudu-gudu zai shiga jirgi har ya biya kuɗin jirgi yayi komai zai shiga kwatsam yaji an riƙe masa riga ta baya an jawo shi da ƙarfin gaske, a razane Sauro ya juya yana kallon wanda ya jawo shi ganin macece yasa ya ajiye jakarsa a gefe yana shirin naɗe hannun rigarsa yana dariyar mugunta yace "wato kece kike bin diddigi nah ko? toh yanzu zan sumar dake nayi tafiyata.." Angel itama murmushi tayi tace "ni ba kalar macen daka raina bane, sai dai ka sumar da wacce kaga zaka iya amma not Angela..." Da gudu sauro ya tafo zai kai mata naushi a kayi tayi saurin sunkuyawa ta girbe masa ƙafa ya faɗi ƙasi ta naushe shi a kunci... Shima wuntsilar da ita yayi ya harɗe mata sawayenta da ƙafarsa, Ganin yana shirin hawa kanta ne yasa tayi wani irin rigingine ta kama hannunsa ta murɗe da ƙarfin gaske saida hannun yayi ƙara, wannan hannun kam ya rigada ya gurɗe, tashi yayi zai gudu itama ta miƙe ta cabki kwalar rigarsa! juyowa yayi ya kirɓa mata naushi a saitin marar ta, Angel bata san lokacin data kurma ihu ba ta kama mararta ta faɗi ƙasi tana birgima, Shi kuwa sauro har ya zari jakar sa zai shiga jirgi yana shirin tafiya, cikin ƙarfin hali Angel tana daga kwance ta zaro ƙaramin bindigarta ta saita ƙafar sauro ta harbe shi, shima lokaci guda ya faɗi ƙasa yaji shigar harsashi, kama ƙafar yayi yana sowa a wajen, mutane kuwa suna tsattsaye suna kallonsu sai wani ne daga cikin mutane ya ƙira motar police ta sanar musu cewa ana faɗa a airport, nan danan saiga motar police da sauri suka zo zasu kama Sauro da Angel har sun ɗaga sauro zasu saka shi acikin motarsu, sukazo kan Angel zasu saka mata ankwa suna cewa "waya bata izinin yin harbi sannan suna tuhumarta da cewa waya bata bindiga inba ita ƴar fashi ba ce, duk basu san ko ita wacece ba, basu san ita soja bace, saida wani daga cikin police ya finciki hannunta zai sanya mata ankwa ta zamar da hannun ta zabga masa mari a fuskarsa ta hankaɗashi gefe, gaba ɗayansu police saida abun ya basu mamaki waran su uku sukayo kanta da sandarsu zasu kai mata duka duk su ukun ta girbe musu ƙafafuwa tana daga kwance domin ta kasa tashi tsabar ciwon da marar ta yake yi mata, Ogan ƴan sanda ne yaje gabanta ya sunkuya yana busa mata hayaƙin tabar da yake zuƙa ya zaro ƴar ƙaramar wuƙa tareda kai hannunsa ya cafki sumar kanta ya ɗora wuƙar a saitin wuyanta yana faɗin "idan kika kuskura kika motsa saina yanke miki maƙogaro, shin ke ɗin ƴar fashi da makami ne? waye oganki? wannan bindigar aina kika samo shi, babban laifi kinyi harbi a cikin mutane...." kafin ya ƙarasa maganar Angel tayi saurin murɗe masa hannu mai wuƙar ta karɓa ta caka masa akan takalminsa mai sahu ciki har saida wuƙar ta ratsa cikin takalmin ta samu ƙafarsa, ihunsa kawai ake sauraro a gurin tace "banida lokacin baku amsa ƙananun ƙwari kawai..." suna cikin wannan halin saiga motar D.P.O da wasu ƴan sanda, daƙer Angel ta miƙe tsaye idonta duk ya rine, wasu police ne sukazo gabanta zasu kai mata hari! ta ciro card a aljihunta ta nuna musu lokaci guda kuwa suka tsaya cak suna bin card ɗinta da kallo sai ɗaya daga cikine yace "Soja ce wallahi..." kafin su rufe baki saiga motar Sojoji sun kai uku suka diddirƙo da manya-manyan bindigoginsu suka tsattsaya saiga Ogah Junaid shima ya fito yana sanye da wandon Soja da kuma farar riga t-shirt yaje gaban Angel ya yi mata ɗaukar luɗa yana ɗauke da ita yace wa D.P.O "she's a commander of soldiers, California Army..." yana kaiwa ƙarshe maganar sa yayi gaba da ita ya buɗe cikin mota ya kwantar da ita a back seat, duk abunda ya faru akwai wani abokin Junaid wanda yake wajen yayi video ya turawa Junaid, shiga cikin motar yayi shima yaja motar ya tafi da ita gida, har wannan lokacin cikin Angel bai daina ciwo ba, saiji tayi yace "nace miki ki tafi da wasu Soja ku kamo mutumin amma kin tafo ke ɗaya ai dole ya raina ki..." Sauran Sojojin kuma jawo Sauro sukayi daga cikin motar police suka sakashi a cikin motarsu suka tafi, Ƴan sandar dake wajen basuyi mamaki ba saboda yanda sukaga Angel tana faɗa har cakawa Ogansu wuƙa tayi a ƙafa daman sunyi zargin tanada wani muƙami... ******* Ayush sauƙowa falo tayi ta samu Mommy tana jera kuloli akan dinning daman yunwa take ji kuma saita fito a daidai, Mommy tana ganinta tace "ha'a Ayushert kin fito ne, gashi kuwa na kammala girkin zo ki zauna ki ci ko.." Ayush kasa magana tayi sai dai ta nufi dinnig ta zauna a kujera, ga tabo a goshi yanda Junaid ya buga mata shi ajikin bango, Mommy cikin tausayawa take kallon Ayush tana maganar zuci "kin kusa ki huta Ayush gobe Junaid zai tafi kafin ya dawo kuwa zan gama saita komai.." ta zuba wa Ayush a plate tace "gashi nan Yarinyar kirki kici kisha magani ko saboda ciwon goshinki..." Ayush ɗaga mata kai kawai tayi tareda ɗago da spoon zata sa abinci a baki, Dai dai lokacin da Junaid ya shugo falo yana ɗauke da Angel, Mommy na ganinsu a haka tace "subhanallahi meya faru da ita?.." Kwantar da ita Junaid yayi akan doguwar sofa yace "rigima tayi da wani yayi mata duka.." ya ƙarasa maganar tareda nufar gurin dinning domin yunwa yake ji, har saida ya zauna zai zuba abinci ya lura da Ayush, ɗagowa yayi yana kallonta, itama kallonsa take cike da fargaba da tsananin tsoronsa domin ta tabbatar yanzu Junaid ba ƙaunarta yake ba tinda har ya furta da bakinsa... Kawar da kansa yayi gefe yana ɗan ƙwala spoon akan glass table sai yake ɗan bada sound yana ɗan cije maroon lips ɗinsa ya ambaci sunanta a hankali "Yushert..." kallonsa kawai take domin tin zuwansa gurin ta dakatar da cin abincin, yace "wacece ke?.." wani irin tambaya yayi mata wanda ita kanta saida ta ɗan razana, still kallonsa take ta kasa buɗar bakinta, yace "Yushert abunda banaso kenam idan nayi wa mutum magana ɗaya inaso ya amsa mun ne akan lokacin, ki kwantar da hankalinki magana nake so nayi dake ta fahimtar juna, ki faɗa mun gaskiya bana son ƙarya da salon yaudara..." Ayush hawaye ta fara zubar wa domin tasan maganar bazai wuce akan video nan ba, tana cikin wannan tunanin taji yace "wacece wannan matar mai niƙab wacce tazo a ranar shagali na??" Gaban Ayush ne yayi matuƙar bugawa da ƙarfin gaske sai wani daram-daramm kake ji, sauran kaɗan ya hana zuciyarta bugawa, ta zaro ido waje ta kafe shi da kallo.. Shima kallonta yake yi yace "ina jinki..." Girgiza masa kai kawai tayi babu bakin magana, ya kuma cewa "Yushert wacece matar nan da kike ƙiranta da Uma?..." nan ma shuru tayi mishi girgiza masa kai kawai take, Jinjina kai yayi ya kawar da kansa gefe cike da takaici domin ya tsani yayi wa mutum magana ya tsaya yana kallonsa, still juyowa yayi idonsa akan nata ya kuma cewa " Yushert wacece matar da ta ɓace bayan ta fito daga ɗakin ki?.." wannan lokacin kam Ayush har da sakin fitsari tana zaune bata ma san tanayi ba, sai ƙarar zubar fitsarin kake ji yana sauƙa akan tiles tsuuuuuu🤣🤣🤣 Ogah Junaid kam jin sauƙar fitsarin ne yasa ya leƙa ƙasan kujerar da take zaune yaga fitsari yana zuba, shi yayi tunanin kofin ruwane ya zuba daga saman table, ɗagowa yayi yana kallonta cike da mamaki yace "Yushert bakida gaskiya kenam? meye manufarki na zama tareda mu? kinyi ƙaryar cewa bakida kowa ashe ke ba mutum bace, ashe ke ahalin Aljanu ce?, toh meyake tafe dake? inaso in sani yanzun nan.." lokaci guda hawaye duk ya wanke mata fuska, idonta yayi jawur tana lumshe su a hankali domin ita kaɗai tasan irin tashin hankalin da take ciki... ya kuma cewa "Yushert magana fah nake miki.." Ayush ko ƙwakkwaran motsi ta kasa yi.. Ran Junaid ne yayi matuƙar ɓaci ganin tinda ya fara magana ko amsa ɗaya bata bashi ba, Cikin zafin nama Junaid ya ɗaga hannayensa biyu da ƙarfin gaske ya doka a tsakiyar glass table na cin abinci Glass dinning ne yayi wani irin ƙara ya dagargaje, tsabar firgici da tashin hankali da kuma tsoro haka kujerar Ayush ya faɗi ta baya ta doku a ƙasi nan take ta fara wani irin shaƙuwa tana fitar da jini daga bakinta, ta zazzaro ido waje tana kallon sama tana shaƙuwa da ƙarfin gaske ga yanda taketa ambaliyar aman jini... Mommy tana zaune a kujerar da Angel take a kwance duk saida suka razana da jin ƙarar fashewar glass table, a gigice Angel ta miƙe tsaye alokacin ma taji babu ciwon cikin, zuciyar Mommy ne yake bugawa da ƙarfin gaske tsabar tsoritar da tayi duk suka nufi gurin da gudu! Mommy tana faɗin "nashiga uku meya faru kuma du Junaiddd..." Angel ganin yanda Ayush take kwance ido a ƙafe ga shaƙuwarta yanda yake dukan dodon kunnuwansu,. da sauri ta durƙusa tasa hannu ta tallafo kayinta tana ƙiran sunanta "Ayush! Ayush!! Ayushert!!! meya faru da ita haka..." Mommy kam tsayawa tayi tana kallon yanda Ayush take tayi tama rasa yanda zatayi gaba ɗaya ta ruɗe, ta rasa mai zatayi ɗaya... Shi kuwa Junaid yana zaune idonsa akan Ayush ya kasa motsawa shima jikinsa duk yayi weak, ga hannayensa duk sun faffashe sai jinin da yaketa zubarwa, ba ƙaramin ciwo yaji ba... Angel ce tace "Mommy mu gaggauta kaita hospital dan Allah, zata iya mutuwa fah..." agigice Mommy tasa hannu zasu ɗauki Ayush! Junaid ya katse su da cewa "kar ku yadda kuje hospital, ku kaimun ita room ɗina..." Mommy tace "baza mu barta a gida ba, ciwo ba ƙaramin ciwo ba, idan baka sonta toh ni ina sonta, kar ka ƙara shiga shirgin Ayush daga yau! babu ruwanka da ita ko meye zatayi, ai ba kai ka kawota gidan ba kuma ba'ace wannan gidan naka bane gidan mahaifinka ne, idan kuma kana gadara da gidan mahaifinka ne toh zamu fita mubar maka gidan inyaso zanje na sayi gidan da zan zauna da Ayusher....." Mommy tana kuka haka ta ƙarasa maganar tana riƙe da Ayush zasu huce Junaid ya miƙe a tsawace yake faɗin "ita ɗin ba mutum bace Aljanace, bamu san meye manufarta akan mu ba, ta ce batada iyaye ashe ƙarya take iyayenta Aljanu ne..." Angel da jin wannan batun tayi saurin kwantar da Ayush taja da baya tana mammannewa ajikin bango, Angel a rayuwarta bata son shiga harƙar Aljanu, tana mungun jin tsoron Aljanu, a duniyar nan ba abunda tafi jin tsoro kamar Aljanu, lokaci guda jikinta ya fara rawa tana kakkarwa! tinda tayi gamo da Aljani a asalin suffar su marasa daɗin gani daga nan take yawan mafarki mai ban tsoro na Aljanu kuma bata son taji an ambatu sunan Aljanu... Mommy gaban Junaid taje ta tsaya tace "meye hujjarka na cewa Aljana ce? shin kofato ka gani a ƙafarta ne ko meye? toh bari na gaya maka ko ita mayyace mai cin naman mutane zan zauna da ita, saidai kabar gidan nan ko kuma ni nabar maka gidan amma Ayush ba yanda zataje a cikin gidan nan, ƙafarta ƙafata don haka karna sake jin wannan batun a bakinka, Kuma last warning idan ka sake musguna wa rayuwar wannan yarinyar ko kuma ka sake dukanta toh wallahi wallahi saina tsine maka, kuma nabar maka gidan...." Juyowa Mommy tayi ta kama Ayush zata ɗagata tace wa Angel "zo ki tayani mu ɗagata hospital za'a kaita.." Angel tana manne da jikin bango tace "a'ah Mommy bazan iya ba..." muryar ta na kakkarwa kamar mai yin zazzaɓi, Mommy tace "Angel kodai cikin nakin ne?.." dasauri Angel tace "eeeeh ciki nane..." Mommy tace "toh shikenam Allah ya yaye miki.." tayi ƙoƙarin ɗaga Ayush suna tafiya a hankali zasuyi waje... Da gudu Angel ta wuce ɗakinta taje tasa sakata.. Mommy har sun doshi ƙofar fita daga falon taga an ɗaga Ayush sama dasauri ta waiwayo taga Junaid ne ya ɗorata akan kafaɗarsa yana kallon Mommy yace "am sorry Mom banaso akaita hospital kuma du ace mun ta ɓata, ki ƙira Doctor yazo har gida yayi mata magani..." yana kaiwa haka ya juya ya nufi upstairs da ita, kai tsaye room ɗinsa ya shiga.. Mommy tsabar takaici kasa cewa komai tayi sai tsaya kallonsa da tayi har ya kule mata, zama tayi akan kujera tayi tagumi... Lokaci guda ta zabura ta miƙe da sauri taje ta ɗauki phone ɗinta ta ƙira number Doctor Samuel emergency... Tana katse ƙiran tajiyo jiniyar motar sojoji, zama tayi akan kujera bata bi takansu bama, Sojoji guda uku ne suka kawo Sauro bayan sunje an cire masa bullet a ƙafarsa, shugo dashi sukayi kai tsaye part ɗin horo suka wuce dashi, suka zaunar dashi akan chair suka ɗaɗɗaureshi da igiya a jikin kujerar, Sai nishi yake tayi tsabar azabar daya sha a hannun sojojin kafin su kawo shi, suna gama aikinsu sukayi tafiyarsu, daman Ogah Junaid yace musu a gidansa zai hukunta shi... Sojojin nan suna tafiya saiga motar Doctor Samuel ya tafo da kayan aiki, Angel ce ta fito da gudu ta wuce Mommy a falo ta fice waje, Mommy sake baki tayi tana kallonta tace "ohhhh mai ciwon ciki..." Angel tana fita taci karo da Doctor Samuel bata tsaya bin ta kanshi bama tayi wucewar ta, shi kuwa kallonta ya tsaya yi har ta ƙule masa amma bai daina leƙenta ba har yaje ya gwara kansa ajikin bango bai saniba, saida ya bugu tukun ya dawo hayyacinsa ya shige falon.. Ita kuwa Angel gurin sauro taje tana zuwa ta cankeshi da ƙafa saida ya dungura, duk fuskarsa ya kumbura tsabar mazgar daya sha, ɗago kansa yayi ganin Angel ce kawai ya fara tintsirewa da dariya irin mai ƙona rai ɗin nan, Angel ta gama fusata haka ta ɗauki wani katako ta fara jibga masa amma bai daina dariyar ba, duk da yana jin zafin dukan amma bai nuna mata ba haka yaketa mata gwaliyo yana dariya, yana mata hakane saboda ya ƙuntata mata... ****** Bayan Doctor Samuel da mommy sun shiga ɗakin Junaid! tarar dashi sukayi yanata danna ƙirjin Ayush, ya buɗe bakinta yana hura mata iskar bakinsa sakamakon rashin numfashi, Ga yanda jini yake fita daga bakinta amma haka yake haɗe musu baki guri ɗaya yana hura mata iska, Shima bakinsa yayi baje-baje da jinin bakin Ayushh 🤮🤮🤮🤮🤮🤮 Mommy da Doctor haka suka tsaya suna kallon ikon Allah, shi Junaid bai ma san sun shugo ba, saida ya ɗago tukun yayi ido huɗu dasu kana ganin shi kasan akwai damuwa a tattare dashi, A fusace ya dakawa Doctor tsawa yana faɗin "toh tsayuwar mai kake yi, kazo ka dubata! banaso na rasata domin ita ɗin bugun zuciyata ce..." Doctor dasauri yayo kan Ayush yana dubata ɗagowa yayi yace "batada jini pah.." yayi maganar ta harshen turanci, Junaid miƙa masa hannu yayi yace "gashi kayi sauri ka ɗibi jinin..." Doctor da saurinsa ya nemo allura da ledar saka jini ya soma jan jinin Junaid saida ya ɗebi leda guda na jini, tukun ya ɗaurawa Ayush! Junaid ana gama ɗebe masa jini ya shige toilet ya wanke jinin bakinsa yayi brush tukun ya fito yayi ficewarsa acikin ɗakin... ______________ Angel kuma tana nan tana ta faman dukan mutuminta shi kuwa bai daina mata dariya ba, dukansa take shi kuwa dariya yake mata duk ta faffasa masa jiki, duk abunda yake yi kuwa Ogah Junaid yana tsaye a bakin ƙofa yana kallonsu, Angel har da kukanta tsabar takaici sai dariya yaketa mata, Junaid ƙarasa shugowa yayi yazo gaban Sauro ya tsaya, alokacin ne Angel ta dakata da dukansa, shi kuwa Sauro ganin Junaid yasa yayi shuru da yin dariyar yana zazzaro da idanuwansa, Junaid hannu yasa ya ɗago kujerar Sauro ya zaunar, shima kujera ya jawo ya zauna yace wa Angel ta miƙo masa jakar gefenta, acikin jakar kuwa tarukucen kayan horo ne har da su guduma ta miƙo masa ya ɗauko wani ƙaton almakashi na ƙarfe mai kaifin bala'i! Sauro yana ganin ƙarfen da yake hannun Junaid ya fara zaro ido waje yana fitar da gumi, Itama Angel tana tsaye tanason ganin shin wani irin hukunci Ogah Junaid zai aikata, Fuskar Junaid ko Annuri babu haka ya kamo hannun Sauro ya saita ƴar ƙaramar yatsansa tin daga dungun da wannan ƙaton almakashin ya datsa yatsar, Wani irin ihu Sauro ya ƙwallla su mommy suna can cikin ɗakin Junaid saida suka razana da wannan ihun, Itama Angel rufe idonta tayi sosai bata son ganin wannan hukuncin, Ɗan ƙaramin yatsar Sauro ne ya faɗo ƙasi, yatsunsa sun zama guda huɗu kenam, Haka Sauro yake ihu kamar ransa zai fita, haka Junaid ya kamo ɗayan hannunsa yana ƙoƙarin yanke ƙaramin yatsar kuma du, Haka Sauro yake magiya yana roƙonsa akan ya kyale shi haka, roƙonsa yake yana haɗashi da girman Allah yace "wallahi tallahi Lailah ce ta sakani amma ni bansan yarinyar bama sai a lokacin, Lailah ce ta bani dubu hamsin tayi mana video bayan ta bata ƙwayar maye da kuma tada sha'awa, amma banida laifi kayi mun rai Ogah Junaid...." Itama Angel riƙe kafaɗar Junaid tayi tace "kayi haƙuri My man hukuncin yayi tsauri ka barshi haka, ka gundule masa yatsa ɗaya ka temaka karka yanke ɗayan..." Junaid baice musu komai ba haka ya miƙe yana ƙoƙarin ficewa yace wa Angel "ki kunce shi yayi tafiyarsa idan zai iya, idan kuma bazai iya ba sai ki sa a nemo tifa a ɗauke shi... Daga nan yayi ficewarsa..... *DAN ALLAH KUYI MUN COMMENTS IRIN NA JIYA, ALLAH JIYA NAJI DAƊIN COMMENTS ƊINKU...* *MASU FITA YAƘI KU AJIYE KAYAN YAƘI TUKUN DOMIN AN ƊAGA TAFIYAR SAI AN HUKUNTA LAILAH🥹🥹🥹🥹🥹🥹🥹🥹* 𝑡𝑦𝑝𝑖𝑛𝑔✍️ 𝗠𝗔𝗧𝗔𝗥 𝗗𝗔𝗠𝗨𝗦𝗔 the wife of a tiger🐅🐅🐅🐅 𝙼𝚊𝚕𝚕𝚊𝚔𝚒𝚗 𝙰𝚜𝚖𝚎𝚎𝚝𝚊𝚑 ✍️✍️ 𝙿𝚊𝚒𝚍 𝚋𝚘𝚘𝚔 𝚌𝚊𝚕𝚕 𝚘𝚛 𝚠𝚑𝚊𝚝𝚜𝙰𝚙𝚙 09065443871 *💫💫{{N W A}}💫💫* Book two C̶h̶a̶p̶t̶e̶r̶ 21 ➡️ 22 Junaid fitarsa daga gida kai tsaye gidansu Lailah yayi, yana zuwa ƙofar gidan ya sauƙo daga cikin motarsa ya fara knocking da ƙarfin gaske, maigadi ne ya buɗe yana masifar "wai waye wannan baƙon buga gate ne? haba jarababbu kawai.." yana buɗewa yayi kucuɓus da Oga Junaiddd yanata huci, maigadi zaro eyes yayi waje jikinsa na ɓari yake furta "innahu min sulaimanu wa innahu Bismillahi rahmanu rahiiiim, ƙalu innalillahi wa inna ilaihi raju'unnnn...." bai ƙarasa addu'ar ba Junaid ya zabga masa wani irin gigitaccen mari har saida ya dungura, yayi wucewarsa ciki ba excuse.. yana zuwa ya tura ƙofar falo cikin sa'a kuwa yaci karo da Lailah tana kwance akan kujera tana chatting, jin bugar ƙofa yasa ta tashi a razane tana bin Junaid da kallo, wani irin haɗiyar yawu tayi tana girgiza kai tareda faɗin "Ogah Junaid.." wani irin tsawa ya daka mata yace "shut up! bana buƙatar jin kalmar ki ko ɗaya..." yasa hannu ya finciko ta yana janta zaiyi waje da ita, Ihu Lailah ta fara kurmawa cikin ƙarfin hali ta zame hannunta ta miƙe da gudu ta nufi ɗakinta, shima binta yayi yana cewa "yau ba abunda zai hana na hukunta ki Lailah, zan kaiki can gidan mu..." turo ƙofar ɗakinta tayi zatasa key daiden lokacin ya ƙaraso da ƙarfin gaske ya tura ɗakin saida ta hautsina ƙasi tsabar bugar da ƙofar yayi mata, tana kuka tana magiyar "dan girman Allah Ogah Junaid ka kyaleni na tuba, wallahi bazan ƙara ba.." ɗagota yayi daga ƙasin ɗakin ya wurgata saman gadonta sannan ya juya ya rufe ƙofar ɗakin yasa key tareda juyowa yaje bakin gadon yana daga tsaye ya ɗora ƙafarsa ɗaya akan gadon, ƙafa ɗaya kuma a ƙasi ya riƙo ƙafar Lailah ya jawota gabansa tareda zaunar da ita yayi mata alamar tayi shuru yatsarsa akan lips ɗinsa yace "shiisssh kimun shuru, idan kuwa ba haka ba zan ƙwaƙule miki eyes yanzun nan..." Lailah da sauri tasa hannunta ta rufe bakinta tayi shuru gurin yayi tsitt kamar ba mutane a ɗakin, ga gumin da yaketa yarfo mata, shi kuwa binta yake da kallo cikin ɓacin rai yace "meyasa kika aikata hakan? amsa ɗaya zaki bani..." Ita kuma Lailah sanin halin Junaid yasa bata tsaya masa wani inda-inda ba tayi saurin cewa "wallahi saboda inasonka ne, ina bala'in kishinka...." bata ƙarasa maganar ba ya daka mata tsawa tareda faɗin "you're an ingratitude fool Lailah, saboda kina sona shiyasa zakiyi haka? toh da kikayi hakan shi zai sa na soki kenam?..." Girgiza kai tayi a tsorace, hannu yasa a cikin aljihun wandonsa ya ciro wata ƴar ƙaramar wuƙa yana goge ta yace "ai saboda kinada idanuwa ne yasa kike aikata haka ko, toh yanzu zaki rabu da eyes ɗinki sai muga yanda zakiyi munafurci zuwa gaba..." Lailah ganin Junaiddd yana saito mata wuƙa saitin idonta yasa tayi saurin sumewa a wajen ta faɗi a saman gadonta ta baya, Sauƙe numfashi yayi yana kallonta, miƙewa yayi ya ɗauko bottle na ruwa akan mirror yazo yana watsa mata ruwan a kan fuskarta a gigice ta farfaɗo tana sauƙe numfashi sama-sama, ganin fuskar Junaid yasa ta ƙara komawa sumar still ya ƙara watsa mata ruwa ta tashi zaune, kuma du ta juyar da idonta zata ƙara sumewa a tsawace yace "wallahi tallahi kika ƙara kwanciya mun saina faffasa miki ido da wuƙannan, a tsorace ta dakata jikinta na kakkarwa ta buɗe baki zatayi kuka ya ɗauketa da wani irin gigitaccen mari a gigice ta tashi da gudu ta nufi bakin ƙofa yayi saurin riƙe rigarta ta baya cikin rashin sa'a kuwa rigar ta ɓere gaba ɗaya tsabar riƙon da Junaid yayi mata, fincikota yayi zai wullata saman gado shima ƙafarsa ta harɗe suka faɗi a tare kan gadon, yana saman kanta suna fuskantar juna, Lailah riga ya yage daga ita sai breziyya, rufe ido Lailah tayi sosai jin yanda Junaid ya faɗo mata a jiki! jin shurun yayi yawa ne yasa Lailah buɗe idonta a hankali, gani tayi Ogah Junaid ya kafa idonsa akan ƙirjinta ko motsi ya gagara yi, ita kuwa ganin haka yasa tasa hannu ta bayanta ta ɓalle rigar brezy ɗin ta saiga manya-manyan breast ɗinta sun wantsilo, ganin haka yasa Junaid ya ɗago yana kallonta cike da mamaki yace "Lailah are you stupid?..." dogon tsuka yaja sannan ya ɗago daga kanta yana faɗin "bazanyi mamaki ba duk abunda akace kinyi, look bafa nayi miki hakane don saboda na rikice ba, nayi miki hakane saboda naga kalar taki tarbiya, yarinya ba kunya..." tashi tayi a tsorace kamar zatayi kuka tana ƙoƙarin rufe jikinta da rigarta, tace "dan Allah Ogah Junaid kayi haƙuri..." Murmushi yayi sannan yace "Hmmm! Lailah kenam..." yasa hannu yana ƙoƙarin cire belt ɗin kunkuminsa, zaro ido Lailah tayi tace "dan Allah Ogah Junaid kar kayi mun fyaɗe..." wani irin abu yaji ya daki zuciyarsa ya zaro ido waje cike da mamaki yace "whattt! raping? very stupid..." fuska ba Annuri haka ya zaro belt ɗinsa ya fara dukanta cikin ɓacin rai, jin sauƙar dukan yasa ta tashi a gigice tana ihu tareda sosa jikinta, ga riga ya sulale ƙasi, breziya ya faɗi shima jikinta ba komai sai dogon wandon dake jikinta, haka yaketa dukanta kamar bazai barta da rai ba, duk saida ya faffasa mata jiki, acikin tana ihu har ta komo muryarta ya disashe kukan baya fitowa saida ya gama bata kashi a hannu tukun ya ɗauki rigarta ya ɓeɓɓera mata shi yayi igiya da rigar sannan ya ɗaure mata ƙafafu, yazo kan hannayenta suma ya haɗesu ya ɗaure guri ɗaya, ya janyo kujerar mirror ya taka ya tsaya sannan ya wurga igiya saman fankar ɗakin ya ɗaure sosai, ya sauƙo ya ɗauki Lailah a kafaɗarsa ya sake hawa saman kujerar ya kuma ɗaure mata ƙafa da igiyar panka ya sauƙo ya barta a sama tanata ihu, ƙafafunta sune a sama, kayinta kuma yana kallowa ƙasi sai lilo take tayi a sama, Juyawa yayi har zai fita ya sake juyo wa ya ɗauki breziyar ta ya sake hawa kujerar ya rufe mata ƙirjinta sannan yasa gam ya manne mata bakinta, ya sauƙa yana cewa "tinda ke bakida kunya toh ni yau zan nuna miki yanda ake asalin rashin kunya wawiya kawai..." yana kaiwa nan yayi ficewarsa.. ______________ Bayan Doctor Samuel ya gama treat ɗin Ayush tafiyarsa yayi, Mommy kuma ɗakin horo taje ta dubowa meke faruwa duk da tasan aikin Junaid ne, shi inbaiyi mugunta ba baya jin daɗi... tana tsaye a bakin ƙofar ɗakin tana kallon mutumin da Angel take since masa ɗaurin igiya, Mommy ganin yanda jini yake malala a ƙasin tiles a ruɗe tace "Innalillahi wa inna ilaihi raju'un, Angel meya faru dashi ne haka nake ganin jini kamar bazai rayu ba?..." Angel tace "Hmmm Mommy kenam wannan babban mai laifi ne, ya cancanci wannan hukunci ne, abunda yasa zakiga zubar jinin yayi yawa na farko na harbe masa ƙafa da gun, na biyu kuma Ogah Junaid ya gundule masa ƴar yatsaa...". Angel ta ƙarasa maganar tana kwashewa da dariya.. Dogon tsuka Mommy taja tana faɗin "kenam abun dariya ne wannan? wai meyasa bakuda imani ne dake da Junaid? especially shi Junaid zuciyarsa kamar bana musulmai baa.." Mommy shuru ta ɗanyi ganin yanda Angel ta haɗe rai tana fushi tace "kenam Mommy musulmai ne kawai masu imani?...." Mommy tace "Ahh musulmai ne mana masu imani Angel, masu imani sai musulmai waɗanda sukayi imani da Allah da manzonninsa da mala'ikunsa da litattafansa da ranar tashin alƙiyama da kuma imani da ƙaddara mai kyau ko marar kyau..." Angel fashewa tayi da matsanancin kuka ta miƙe tsaye tana faɗin "shikenam tinda ni banida Imani.." tayi ficewarta da gudu ta nufi falo... Mommy sake baki tayi tana kallonta tace "Ohh kenam bazan faɗi gaskiya ba? saina mutu da a faɗi gaskiyar? toh dole na faɗi gaskiya tinda kin ƙi musulunta! na gaya miki Jesus ba Allah bane, mu awaran mu manzon Allah ne Annabi Isah...." haka Mommy ta rinƙa masifa, tazo kan Sauro tana faɗin "bawan Allah sannu ko! Allah Sarki saboda rashin tausayi a cirewa mutum ɓangare na jikinsa haba..." Haka Mommy tasa hannu ta tallafawa Sauro ya tashi yana ɗingishi daƙer, haka mommy ta shigar dashi falo ta kaishi har ɗakin medicine zatayi masa magani ta tsayar masa da jinin... Angel kai tsaye ɗakin Junaid taje ta tana kuka ta samu Ayush an ɗaura mata ledar jini, bata bi ta kanta bama haka ta durƙusa a ƙasi ta kifa kanta tana ta sharar kuka haɗe da magana tana faɗin "ni duk sanda nazo ƙasan nan sai mommy tamun gorin musulunci, naga nima inada addini na, wai meyasa mommy take mun hakane, wallahi nima dole na musulunta a wannan lokacin kam! taya zan fara fuskantar musulunci..." duk wannan maganganun da Angel takeyi kaf a kunnen Ayush domin ta daɗe da farfaɗowa, a hankali Ayush ta buɗe idonta tana kallon yanda Angel take a kife a ƙasan carpet, Ayush daƙer take motsa lips ɗinta ta furta "Aunty Angela..." Angel dakatawa tayi da kukan jin an ƙira sunanta, ta ɗago tana kallon Ayush cikin mamaki tace. "daman kin farfaɗo ne Ayush?..." Ayush tace "ehh Aunty Angela, duk naji abubuwan da kike faɗa! nima inaso ki musulunta, wallahi Aunty Angel musulunci akwai daɗi, ki musulunta mana, Mommy masoyiyarki ce shiyasa take miki akan ki musulunta..." Angel jinjina kai tayi tace "shikenam Ayush zan musulunta da izinin Allah, amma saidai bansan yanda zanyi na musulunta ba..." Ayush tace "karki damu duk wannan mai sauƙi ne indai har kinsa a ranki zaki musulunta da gaske saboda shi Allah mu yana aiki ne da zuciya...." Murmushi Angel tayi sannan tace "har cikin zuciyata inaso na musulunta Ayush..." Ayushert tace "karki damu Aunty Angel zan kaiki wajen wani babban malami zaki musulunta a hannunsa..." Angel tace "please Ayush zamu iya zuwa gurin malamin a yau ko? saboda kinga gobe da asussuba zamu tafi headquarters, anan za'a turo mana jirgaye suzo su ɗauɗauke mu, gobe insha Allahu zamu kwana ne a ƙasar California, Ina tunanin idan muka kammala yaƙin mu zan iya dawowa na ƙara hutawa kafin nan ki koya mun abubuwan da musulunci yake ƙunshe dashi, sannan ki koya mun wannan karatun da kukeyi a sallah, ki koya mun sallah! idan na gama koya saina koma gurin aikin soja na..." Murmushi Ayush tayi itama tace "indai kin musulunta kam za'a koya miki komai Aunty Angel, Amma inaso idan kun kammala yaƙinku ki ajiye aikin soja kema kiyi aurenki..." Angel tunani ta shiga yi daga bisani kuma tace "bana tunanin aure araina Ayush, shima kanshi Junaid bawai son Aurensa nake yi ba no he is my Besty, Amma zanyi tunani akan maganar ki saidai kuma ina tsoron komawa ƙasarmu saboda iyayena bazasu yadda akan karɓar Musulunci danayi ba..." Ayush ta tari yawunta tace "saiki dawo gurin mommy ki zauna, zakiga mijin Aure yazo miki..." Angel murmushi kawai tayi ba tareda tace komai ba... Ayush ce ta ɗan motsa tana ƙoƙarin tashi zaune taji an daka mata wani irin gigitaccen tsawa kamar daga sama, a firgice Ayush ta saki ƙara jikinta na ɓari tayi matuƙar tsorata sosai dajin tsawar, Ba Ayush ba hatta Angel saida ta tsorata sosai da sauri ta waiwaya bayanta! Junaid ne ya shugo yana nuna Ayush da ɗan yatsansa yana faɗin "kinada hankali kuwa Yushert? jini pah aka ɗaura miki amma kina ƙoƙarin tashi, kinsan irin matsalar da zaki samu kuwa idan jinin ya kauce hanya?..." Angel tace "haba My man, wannan tsawar ai saika ƙara firgitar da ita yanzu ma ba lafiya ne da ita ba..." Junaid juyowa yayi yana kallon Angel yace "meyasa lokacin da take ƙoƙarin tashi baki mata magana ba?..." tace "toh ni ban lura da ita ba..." yace "Okay toh tashi ki bani guri inason magana da ita.." Angel tashi tayi tana ƙoƙarin tafiya! Ayush tayi saurin dakatar da ita tana kuka tace "dan Allah Aunty Angel karki tafi ki barni wallahi kasheni zaiyi, banason kasancewa da shi, ki temaka mun..." Angel kallon yanda Junaid yake zaune a bakin gado tayi tace "Ogah Junaid kaga irinta koh? ta fara fitar dakai daga cikin ranta, ko yaro ne yau da gobe ana masa tsawa dole zai gujeka balle ita data mallaki hankalin kanta, dole zatayi tunanin baka ƙaunar ta...." rufe idonsa yayi yace "Please Angel leave my room, kar raina ya ɓaci..." kamar zatayi kuka haka Angel tabar ɗakin, itama har cikin zuciyarta Junaid ya fara fita mata a rai saboda wannan tsawar da yake yi da kuma miskilanci irin nashi... Ayush sunkuyar da kanta tayi ƙasi tana zubda hawaye tareda fargaban tambayoyin da zai ƙara yi mata, Junaid yana kallon gabansa yace "ya jikin nakin?.." shuru tayi bata bashi amsa ba, still kanta a sunkuye ko ɗagowa batayi ba. Junaid yace "magana nake miki Yushert, kar kiyi tunanin zan barki ne akan wannan maganar da na fara miki tambayoyi akansa domin hankalina bazai taɓa kwanciya dake ba indai baki sanar mun ainihin ko ke wacece ba..." Ayush still bata ɗago da kanta ta kalle shi bama balle ta bashi amsa, ita batama san mezata ce masa ba... Ya kuma cewa "kaina a ɗaure yake kuma ke kaɗaice zaki iya warware mun, shin wacece wannan Uman nakin? a wace duniya take? shin mutum ce ko Aljana? sannan ke kanki mekika zo yi gidan nan? Ina jiran amsar ki yanzun nan, duk waɗannan tambayoyin ba masu wahala bane indai kinada gaskiya..." Ayush ɗagowa tayi tana kallonsa da idanuwanta waɗanda sukayi jajawur tsabar baƙin ciki da kuma kukan data sha, murya ciki-ciki tace "Yaya Junaid kayi haƙuri waɗannan tambayoyin bazan iya amsa maka su ba, Kamar yanda na gaya muku ni marainiya ce..." da sauri Junaid ya juyo yana kallonta cike da takaici yace "ƙarya kike Yushert, ki faɗa mun gaskiya karki raina mun wayo..." Ayush tace "Yaya Junaid mai kake so nace maka..." Junaid wani irin kallo ya watsa mata yace "Yaushert bana son shirme fah, nace ki gaya mun wacece ke? banason munafurci da iskanci nasan akwai abunda yake cikin zuciyarki..." Ayush ranta ne ya ɓaci ta zare allurar jinin da aka ɗaura mata ta sauƙa daga kan gado tace "wai shin Yaya Junaid kai ka kawo ni gidan nan ne? meyasa kake son takura mun ne? dan Allah ka rabu dani na roƙe ka, idan kuma baka son zama na agidan nan to ni yau zan bar muku gidan, na gode Allah tinda har ka samu lafiya...." tana kaiwa nan tayi ficewar ta, ga sauran jinin da ta bar masa. Junaid buɗe baki yayi yana kallonta har ta fice, yayi mamakin jin kalaman nan daga bakin Yushert, dafa kansa yayi yana hura iskar bakinsa tsabar tsananin ciwon kai da yake damunsa,. Maimaita maganar ta yayi cewa "kin gode Allah tinda na samu lafiya?..." Abunda ya tsaya masa arai kenam... Ita kuwa Ayush tana zuwa ɗakinta ta ɗauki hijab ɗinta ta saka ta jawo jakarta tana kuka ta fice a ɗakin, Daman kayanta a shirye suke dasauri ta sauƙa daga down stairs, ta fice a falon! gudu-gudu sauri-sauri haka Ayush ta nufi gate tana jan akwatinta, Shi kuwa Junaid yana tsaye ta window yana kallonta.... 𝑡𝑦𝑝𝑖𝑛𝑔✍️ 𝗠𝗔𝗧𝗔𝗥 𝗗𝗔𝗠𝗨𝗦𝗔 the wife of a tiger🐅🐅🐅🐅 𝙼𝚊𝚕𝚕𝚊𝚔𝚒𝚗 𝙰𝚜𝚖𝚎𝚎𝚝𝚊𝚑 ✍️✍️ 𝙿𝚊𝚒𝚍 𝚋𝚘𝚘𝚔 𝚌𝚊𝚕𝚕 𝚘𝚛 𝚠𝚑𝚊𝚝𝚜𝙰𝚙𝚙 09065443871 *💫💫{{N W A}}💫💫* Book two C̶h̶a̶p̶t̶e̶r̶ 23 ➡️ 24 Doctor Hasheem ne ya shiga falo da sallama a bakinsa gani yayi falon yayi tsit ko motsin mutum babu, haka ya wuce ɗakinsa yaje ya rage kayan jikinsa ya shige toilet yayi wanka ya fito ya sanya ƙananun kayansa na zaman gida tukun ya fito falo ya wuce kitchen domin ba ƙaramin yunwa yake ji ba, haka yaje ya samu kitchen wayam ba'a yi girki ba, taɓe baki yayi yace "wato yarinyar nan tana can tana ta faman shan baccinta bata samu damar yimana girki ba kenam, zanje na sameta dan ƙaniyarta..." ficewa yayi daga kitchen rai a ɓace ya nufi ɗakin Lailah! yana zuwa kuwa ya buga ɗakin da ƙarfin gaske ya buɗe baki zaiyi masifa yaga abu a sama yanata lilo, sake baki yayi yana kallon ikon Allah, saida yasa hannu ya murƙusa idanuwansa sosai yana kallon Lailah wacce take rataye a saman fanka ga kuma jikinta duk ya farfashe dake daga ita sai breziya... A tsorace ya furta "Lailah?..." Shuru bata amsa ba sakamakon sumar datayi, a ruɗe ya jawo kujerar mirror ya hau ya sinco ta ya sanya mata riga, da gudu ya fice a ɗakin yaje ya ɗauko box na magani tareda bottle na ruwan sanyi ya dawo ɗakin Lailah, harda hawayensa sam baiji daɗin ganin Autarsu a cikin wannan halin ba, haka ya shiga yayyafa mata ruwa a gigice kuwa ta farfaɗo tana faɗin "dan girman Allah Ogah Junaid kayi mun rai, wallahi bazan sake ba, dan Allah ka ƙyaleni haka wayyo mutuwa zanyi..." Doctor Hasheem jin abunda Lailah take faɗa ne yasa ransa yayi matuƙar ɓaci yace "Junaidd ne yayi miki wannan aikin?.." Lailah tana fitar da numfashi daƙer ganin Yayanta ne yasa ta rungumeshi tana kuka sosai tareda faɗin "Yayana wayyo Allah, Ogah Junaid ne..." kuka ne yaci ranta sosai, haka Doctor Hasheem yake bubbugar bayanta a hankali yana rarrashinta, shi kaɗai yasan kalar raɗaɗin da yake ji aransa... yana sharar ƙwalla haka yayi treatment ɗin jikin Lailah ya bata magani tasha, gaba ɗaya ta zamo kalar tausayi, idanuwanta sunyi lufu-lufu, kwantar da ita yayi tareda faɗin "bari naje na sama miki abunda zaki ci ko?.." tashi yayi a fusace ya ƙudurta a ransa cewa wannan karan kam bazai ƙyale Junaid ba, saiya je har gida ya sameshi akan abunda yayi wa Lailah... ****** Ayush tana tsaye a bakin gate tanason fita saidai maigadi ya hanata fita sakamakon nunin da Junaid yayi masa daga saman window ya masa alamu da hannu na kada ya barta ta fita, Ayush tayi-tayi akan ya barta ta fita amma maigadi yaƙi, Ayush ce ta lura da yanda maigadin yake kallo, itama ɗaga kanta tayi sama taga Junaid ne ashe ya hana shi buɗe mata, Ayush kamar zatayi kuka haka take jumping da ƙafafunta a cikin ranta tace "wayyo na shiga uku indai ban bar gidan nan ba toh tabbas asirina saiya tonu, kuma ba ƙaramin hukunci Yaya Junaid zai ɗauka ba, nafison kafin su ankare da sanin ko wacece ni nabar gidan kawai..." tana cikin wannan tunani sai ta jiyo Muryar Angel ta nufo gurinta tana faɗin "Ayush yana ganki da akwati lafiya kuwa?..." Girgiza kai Ayush tayi ba tareda ta furta komai ba, Angel ce ta sake yin magana tace "kodai Junaid ne ya koreki?.." Girgiza kai tayi tace "a'ah babu komai.." Angel tace "toh tinda babu komai ki shugo ciki, kin manta zaki rakani gurin malamin da kikace zan musulunta a hannunsa.." Murmushi Ayush tayi tace "a'ah ban manta ba Aunty Angel" Angel tace "to yanzu kuwa zaki rakani muje mu kinga bamuda isasshen lokaci.." Ayush ta amsa mata da "toh.." ta furta hakan tareda ƙara ɗaga kanta sama tana kallon Junaid dake tsaye a window ɗakinsa shima binta yake da kallo... Mommy bayan ta kammala yiwa Sauro magani fito dashi tayi har zuwa bakin gate ta tura maigadi akan yaje ya dubo mata mai keke napep, Sauro zama yayi domin bazai iya juran tsayuwa ba, ita kuwa Mommy sai haƙuri take bashi tana "sannu maza bawan Allah, kana ji kana gani akasa ƙarfe aka cire maka yatsa tsabar rashin tausayi irin na Junaid..." Bayan wasu ɗan mintuna saiga maigadi acikin napep ya ƙirawo shi, daƙer Sauro ya shiga ciki ya zaune, mommy ce ta biya kuɗin napep sannan ta bawa sauro kuɗin kashewa har Naira 100k! Juyawa Mommy tayi zata koma ciki saiga Angel da Ayush sun fito a tare suna shirin shiga mota, Mommy tace "yanzun sai ina?.." Angel tana yamutsa fuska tace "mom zamu je unguwa ne da zarar mun dawo zan sanar miki yanda muka je..." Mommy tace "toh shikenam sai kun dawo Allah yasa muji alheri..." tana kaiwa nan ta shige cikin falo.. Su kuma Angel tada motar tayi ta karya ƙwana ta miƙi hanyar gate, ita Angel tana sanye da Abaya da ɗan gyalensa tasha makeup sosai tayi kyau, ita kuma Ayush dogon hijab tasa mai hannu irin hijabi jalbab ɗin nan amma har ƙasi yake ja, fuskarta a koɗe ba kwalliya, haka maigadi ya buɗe musu suka fice a gidan gaba ɗaya, kai tsaye gidan malam lawan suka miƙa... Suna fita kuwa saiga motar Doctor Hasheem sun ganshi amma basu tsaya sauraronshi ba, parker motarsa yayi daga waje sannan ya fito a fusace ya fara knocking, maigadi ne ya buɗe ganin Doctor Hasheem ne yasa shi faɗin "sannu da zuwa Doctor ka shugo mana.." Doctor Hasheem bai nuna wa maigadi cewa akwai matsala ba sai cewa yayi "yawwa Baba! Junaid kuwa yana ciki?.." Maigadi ya amsa masa da "eh yana nan" Dasauri Doctor ya shige yana sauri har ya iso compound, tsayawa yayi yana knocking ƙofar falo ba jumawa aka buɗe, Mommy ganin Doctor yasa ta murmushi tace "wata sabon gani, wato sai yau aka tuna dani ko.." Doctor yana sosa ƙeya ya gaida mommy sannan ya tambayeta Junaid, Mommy tace "toh ka shugo mana Junaid yana can ɗakinsa..." Doctor Hasheem bai tsaya jin abunda Mommy zatace ba haka yayi saurin haura upstairs yana zuwa kuwa ya tura ɗakin Junaid cikin sa'a kuwa ya sameshi yana kwance, Shima Junaid ɗin ransa ne ya ɓaci domin ko wayene ba'a shugo masa ɗaki kai tsaye ba tareda excuse ba, Doctor Hasheem ne yaje gaban Junaid ya tsaya yana nuna shi da yatsa tareda faɗin "amma kai Junaid wallahi bakada mutunci, kuma ka ban mamaki domin yin faɗa da mace ba jarumta bane hauka ne zalla da kuma rashin ilimi..." Doctor Hasheem a fusace yake maganar domin ransa ba ƙaramin ɓaci yayi ba, shi kansa bai san abunda yake faɗi ba domin idonsa ya rufe... Junaid yana kwance bai samu damar tashi ba haka yana jin yanda Doctor Hasheem ya tsaya masa akai yana gaya masa maganganu marasa daɗin ji! Doctor Hasheem ne ya cigaba da cewa "saboda kai bakada wata ƙanwa ko ƴan uwa shiyasa zakana musgunawa ƴaƴan mutane, toh yau kam na zo maka warning ka fita a harƙar ƙanwata, idan kuwa ka sake sa hannu ka dakar mun da ita toh wallahi tallahi za'a kwashi ƴan kallo domin zan gaya maka maganar da har ka mutu bazaka daina tunaninsa ba, ni ƙanwata tanada mutunci da daraja kuma tanada ƴanci tana kuma da asali da tushe ba kamar kai ba, kai da har yanzu ba wanda yasan tushen mahaifinka balle azo kanka, saboda haka Lailah ta fika a idon mutane, yanzu bana fargaban tunkararka domin a bayane kake tiger amma yanzu you are a real person bana shakkar ka Junaid, abunda kake yiwa Ayush kar ka sake kace zakayiwa Lailah domin ita Lailah tanada wanda zai tsaya mata, ita kuma Ayush rashin gata ne yasa ba'a bi mata hakki, amma a juri zuwa rafi, Ni dai abunda nazo sanar maka shine idan ka sake dukar mun da ƙanwa wallahi saina maka ka a kotu ayi mana shari'a ai dai kasan hukuncin dukan mace, kuma yanzu ma inda ace zan shigar da ƙara akan abunda kayiwa Lailah toh tabbas da saika shiga gidan yari domin ita kotu ba ruwanta da sanin ko kai wayene da kuma matsayinka, kuma idan wani abu ya sake faruwa dani ko ita Lailah kotu zan nufa direct...." Doctor Hasheem yana kaiwa nan ya juya zai tafi... ***** Mommy tana ɗakinta tana waya da wani babban malami akan wani tsararren masallacin data gina, Mommy tana faɗin "Masha Allah naga masallacin ya tsaru sosai, abunda nakeso yanzu inaso a yau ɗin nan a buɗe masallaci da taron ɗaurin Aure..." daga ɓangaren malamin kuma cewa yayi "hakan ma yanada kyau amma Auren wa za'ayi kuma?..." Mommy tace "gaskiya Auren ne ana so ayishi cikin sirri, mutanen da za'a tara ba wani masu yawa ba, guda goma ma sun isa, masallacin ne da ɗaurin Aure nake so a buɗeta bayan an kammala ɗaurin Auren sai a fara amfani da masallacin, zan gayyaci dattijan unguwar nan da abokan marigayi mijina da kuma malam lawan shima duk su halaci gurin ɗaurin Auren..." Malamin yace "toh shikenam ba matsala Hajiya Fatima mudai ba abunda zamu ce miki saidai Allah ya saka miki da gidan Aljanna, kuma kamar yanda kika ce za'a gayyaci malamai dasu halarci masallacin amma tinda kince a yau ake buƙatar ɗaurin Auren insha Allahu da yamma zuwa ƙarfe 5 za'a gabatar da ɗaurin Auren, yanzu dai ƙarfe 3 ne hajiya ki turo mana da sunayen waɗanda za'a ɗaura musu Auren da kuma waɗanda zasu zauna a matsayin wakilansu da kuma sadakin da za'a bayar..." Mommy tace "duk ba abun tashin hankali bane yanzu zanje gidan Barrister Aminu babban abokin mahaifin Angon ne shi zai zamo maɗaurin Auren yaron, Ita kuma yarinyar malam lawan ne zai karɓi Aurenta, don haka zan bada sadakin a Barrister Aminu, nidai malam dan Allah a tabbatar an tara shaidu..." Yace "ba komai hajiya Allah ya sanya alkhairi.." ta amsa da "Ameen.." daga nan suka katse wayar.. Mommy da sauri ta yafa gyalenta ta ɗauki key ɗin mota ta fice a ɗakin.. ***** Angel da Ayush suna tareda Malam lawan sun kora masa bayani kuma ya gamsu yayi gyaran murya sannan yace "insha Allahu zaki musulunta yanzu, zan faɗi kalmar da zaki musulunta wanda idan kika faɗi kalmar shikenam kin shiga cikin musulunci dake da wanda yayi shekara 100 a cikin Musulunci kun zama ɗaya don haka duk abunda nace kema ki maimaita..." Angel tace "toh Malam.." Haka yake karanto mata kalmar shahada tana biyawa har suka zo ƙarshe... Malam yace "yauwa ƴata Masha Allah yanzu kin zama musulma kema, yanzu abunda ya rage shine ki canzawa kanki suna daga Angela ki koma asalin sunan musulmai..." Angel tana murmushi yanzu zuciyarta tayi wasar ta kalli Ayushert tace "meye asalin sunanki Ayush?.." Ayush tace "kina son zama takwarata ne?.." Angel tace "eh mana..." Ayush tayi murmushi sannan tace "wow naji daɗi sosai toh ni sunana Ayshert.." Angel ta turo baki cike da shagwaɓa tace "no no noo ba Aisha ba..." Ayush tana dariya tace "wato sunana ba daɗi ko?".. Angel tace "yess zan zaɓi suna ne mai daɗin gaske..." Malam yace "toh muna jinki ki zaɓi sunan daya kwanta miki..." Angel tajaa dogon numfashi sannan tace "Ni sunana Maryammm na zama takwarar mahaifiyar Annabi Isah..." Sai malam ya ƙarasa mata da cewa "A.S.." gaba ɗayansu sunyi farin ciki sosai dajin sunan da Angel ta zaɓawa kanta.. Malam yace "toh bari na ƙira matata kuje ta gwada miki yanda ake wankan shiga musulunci..." Angel ta amsa da "toh malam.." Malam yana shirin tashi kenam saiga ƙiran wayar Mommy ya ɗaga ƙiran yana faɗin "Assalamu alaikum Hajjajo ykk?.." Mommy ta amsa masa cikin farin ciki sannan ta sanar masa cewa "zuwa ƙarfe 5 na yamma akwai ɗaurin Aure a masallacin data buɗe, ta sanar masa Auren waɗanda za'ayi sannan kuma shine maɗaurin Auren yarinyar..." Malam yaji daɗin wannan batun sosai yayi hamdala sannan yace "ba damuwa Allah ya kaimu lokacin yanzu ma tashi zanyi nayi wankan shirin tafiya don yanzu haka ƙarfe huɗu ne kuma kinga sauran mana awa ɗaya, zan gayyaci mutane sosai..." Mommy ta katse shi da cewa "a'ah malam bana buƙatar wasu mutane da yawa an rigada an tanadar da dattijai basu fi mutane goma zuwa ashirin ba saboda Auren sirri nake son yi wanda banaso ko su yaran su sani balle.." Malam ya jinjina kai tareda faɗin "toh amma Hajiya meyasa? ko basa son junansu ne?.." Mommy tace "a'ah kawai dai akwai abunda nake tsarawa ne, hatta shi yaron bai san da Auren ba balle ita yarinyar kuma banaso a sanar musu dan Allah malam.." Mallam yace "toh shikenam Hajiya ba damuwa Allah ya sanya musu Albarka acikin Auren nan..." Mommy ta amsa da Ameen sannan ta kuma cewa "yanzu haka ina gidan Barrister Aminu shima na sanar masa zaku haɗu a masallacin na bashi sadaki million ɗaya da zoben gwal..." Malam yayi hamdala tareda nuna farin cikinsa daga nan suka katse wayar..." Angel duban malam tayi cike da mamaki tace "malam kamar da Mommy kukayi wayar koh?..." Malam yace "eh hakane Maryam.." ta kuma cewa "toh amma naji kuna maganar Aure shin Auren wa za'ayi?..." Ayush ce ta katseta da cewa "haramun ne shiga shirgin da ba naki ba Aunty Maryam..." Ajiyar zuciya Angel tayi sannan tace "toh na daina ƙanwar Maryam.." Duk sukayi dariya Malam kam girgiza kai yayi yana murmushi sannan ya tashi ya nufi ciki ya sanar da matarsa Malama Zainab akan ta koyawa Angel yanda ake wankan shiga musulunci da duk wani abunda ya shafi Addinin Musulunci.." Malama Zainab ta amsa masa cike da farin ciki itama.... 🗣️🗣️🗣️🗣️ *SANARWA! SANARWA!! SANARWA!!!* *DAN GIRMAN ALLAH KU DAINA COMMENTS A CIKIN WANNAN PAID GROUP, KU RINƘA ZUWA CAN OLD GROUP KUNA COMMENT ACAN SABODA KAR WANCAN GROUP ƊIN YA MUTU KUNGA BA TURA LITTAFI NAKEYI ACAN BA, AMMA YIN COMMENTS ƊINKU ACAN ZAI ƘARA ƘARFAFA GROUP ƊIN...* *NI INA BUƊE GROUP ƊIN NAN NE SABODA ANA ƊANYIN HIRA IDAN AKWAI MASU BADA SHAWARWARI AKAN LITTAFIN SU BADA, AMMA BANDA SHARHI DAN ALLAH ACAN GROUP ZAKUNA YI* *SANNAN WAƊANDA BASA MUN COMMENTS NI BAZANCE MUKU KOMAI BA SABODA KUƊI KUKA BIYA KUKA SHUGO AMMA ZAKU NA GANIN DELAY ƊINA WAJEN YIN NEW UPDATE, DALILIN DAYASA BANA MUKU UPDATE KENAM AKAN LOKACI SHINE RASHIN COMMENTS ƊIN WASU DAGA CIKIN KU...* *WAƊANDA BASA CIKIN WANCAN GROUP ZAN TURO DA LINK KU SHIGA KUNA COMMENT ACAN ƊIN....* 𝑡𝑦𝑝𝑖𝑛𝑔✍️ 𝗠𝗔𝗧𝗔𝗥 𝗗𝗔𝗠𝗨𝗦𝗔 the wife of a tiger🐅🐅🐅🐅 𝙼𝚊𝚕𝚕𝚊𝚔𝚒𝚗 𝙰𝚜𝚖𝚎𝚎𝚝𝚊𝚑 ✍️✍️ 𝙿𝚊𝚒𝚍 𝚋𝚘𝚘𝚔 𝚌𝚊𝚕𝚕 𝚘𝚛 𝚠𝚑𝚊𝚝𝚜𝙰𝚙𝚙 09065443871 *💫💫{{N W A}}💫💫* Book two C̶h̶a̶p̶t̶e̶r̶ 25 ➡️ 26 Junaid yana kwance ya rufe idonsa sosai har wani zaƙami yake yi tsabar ɓacin rai, abunda ya tsara daman a ransa shine idan ya tashi bazai bar Doctor Hasheem da ransa ba, domin babu abunda zai hana shi ya murɗe masa wuya! Doctor Hasheem yayi dace sosai tinda har ya bar ɗakin yayi tafiyarsa Junaid bai buɗe eyes ɗinsa ba, Jikin Junaid ne ya fara kakkarwa, kansa yana juyawa inda ba'a kwance yake ba toh babu abunda zai hanashi faɗuwa, cije leɓɓensa yake da ƙarfin gaske... Shi kuwa Doctor Hasheem sauri-sauri gudu-gudu haka yake tafiya har ya iso bakin gate ya buɗe da sauri ya shige motarsa yabar ƙofar gidan, Ƙarfe 5:00 duk waɗanda aka buƙaci suzo gurin ɗaurin Aure duk sun zo kowa ya halarci gurin sai iya dattijai kawai ake gani dake su aka buƙaci suzo, daga ƙarfe 5 zuwa 6 har an ɗaura Auren Junaid khan Maahmud da kuma Ayshert Máahmud akan sadaki million ɗaya da zoben gwal 🙏🙏 an kammala komai yanzu Junaid da Ayush sun zama ma'aurata a rashin saninsu,. Mommy zuwa tayi ta buga cards na shaidar Auren su da date ɗin da aka ɗaura Auren da photunan ma'auratan a jikin katin, waɗannan katinan ta bugosu ne badan ta rabasu ba sai dan ta ajiyesu ko wata matsala zata iya ɓullowa ga shaida nan, Mommy tayi farin ciki sosai dajin an ɗaura Auren, tuƙin mota take amma bakinta a washe yake ta gagara rufesu tsabar farin ciki, da wannan farin ciki ta isa gida, Horn tayi maigadi ya buɗe mata da sauri domin a lokacin ma ƙiraye-ƙirayen sallar mangarib ake yi, da gudu ta shige gidan kai tsaye wajen parking ta nufa ta ajiye motarta ta fito fuskar nan wasar! Mommy tana shiga ta fara ƙiran sunan Angel! Angel!! Angel!!! "Ha'a kar dai ace yarannan basu dawo ba? kuma dare yayi ai zasu kamo hanya su dawo gida ko?..." tana kaiwa nan ta haura upstairs tana faɗin "bari na dubo yarona ko shima ya fitan ne.." tana zuwa ta fara knocking a hankali har saida ta jera kusan sau biyar tana buga ƙofar ba'a buɗe ba daga baya ta tura ɗakin, ganin Junaid a zaune a bakin gado ya haɗe kansa da gwiwarsa yana rungume da kansa yasa ta cewa "wato kana jina inata faman knocking shine ko ka kulani koh my son..." Junaid yana jinta bai ɗago ba, still ta ƙara cewa "kodai fushi ake da Mommy?..." nan ma ko motsi baiyi ba, hannu mommy tasa tana ƙoƙarin ɗagoshi, ɗagowa yayi da wasu rinannun eyes ɗinsa waɗanda suka shashshanye juyowa yayi yana kallon Mommy ido kamar zai rufe kansa, Mommy cikin nuna damuwa tace "lafiya kuwa Junaid? meya faru dakai haka, dubi yanda ka koma fa..." Murya ciki-ciki yace "Please Mom my Headache..." Mommy tace "subhanallahi ciwon kai kuma my son, meya jawo hakan? bari naje na ɗauko maka magani ko..." tashi mommy tayi da sauri ta fice a ɗakin kai tsaye ɗakin magani ta nufa, ta jido maganunnuwa har kala uku aciki har da wanda zai sakashi bacci domin har da rashin baccin ma, cikin ƙanƙanin lokaci mommy ta dawo hannunta ɗaya yana ɗauke da bottle na ruwa, ta sameshi a yanda yake a zaune itama zaman tayi tana ƙoƙarin ɓare masa maganin, zuciyarsa ne yaketa harbawa da ƙarfin gaske, yana tariyo maganganun Doctor Hasheem, alokacin ne ya gaskaka maganganunsa na cewar bashida ƴanci tinda har ya rasa dangin mahaifinsa, akwai tambayoyin da yakeson yiwa mommy..." yana wannan tunanin Mommy ta bashi maganin data ɓare, karɓa yayi ya watsa su a bakinsa sannan ya karɓi bottle ya korasu da ruwa, sauƙe ruwan yayi yana mai jan dogon numfashi..." Mommy tace "sannu koh my son, Allah ya yaye maka..." Jinjina kai yayi yana kallon ƙasa, Mommy ta kuma cewa "Junaid shin akwai abunda kake ji a ranka akan Ayushert?..." Ɗagowa yayi yana kallonta cike da mamaki yace "bangane ba" Momy tace "ina nufin kana jin sonta a zuciyarka? dan Allah kar ka ɓoye mun ka faɗamun gaskiya..." Junaid ɗan bubbuga goshinsa yayi ido a lumshe yace "kinsan fah a wancan lokacin ma saboda ke ne yasa na amince da baikon nan kuma tazo ta watsa miki ƙasa a ido" yaja dogon numfashi sannan ya kuma cewa "Mom kinsan duk abunda kike so ina ƙoƙarin ganin nayi miki shi, inason ganin abunda zai faranta miki rai..." Mommy tana murmushi tace "Alhamdulillah naji daɗin wannan batu naka, toh amma shin kana jin sonta a zuciyarka? idan nace ka Aureta zaka Aure ta?..." Junaid juyowa yayi yana kallon mommy fuska ba Annuri yana yamutsa fuska yace "wai kam Mom shin ita kaɗai ce mace aduk faɗin duniyan nan? kin nace a wannan yarinyar shin dole ne saina Aureta..." Mommy ta ɗaga kafaɗarta alamar bata damu ba ta kuma cewa "Hmmm Junaid kenam nasan dai kana son Ayush, toh meyasa kake ɓoye mun?..." Junaid yace "toh idan inasonta ita ɗin shin tana sona ne?..." ya ƙarasa maganar ba tareda ya juyo ya kalleta ba... tace "Junaid kenam ai Ayush tafi sonka ma akan son da kake mata sai dai abu ɗayane yasa yanzu bata kula dakai shine ƙuntata mata da kake yi kana nuna mata zafin nama wanda duk son da take maka zata janye ne, tsorone ya hanata ayi muku baiko a wancan lokacin kuma kana dukanta taya zata amince da kai..." Junaid ya ɗan sauƙe numfashi yana murmushi yace "koda ta amince dani ma bazan Aureta ba..." Mommy tace "saboda mai kenam?.." ya juyo yana kallon mommy yace "saboda batada asali kamar yanda nima banida asali toh amma gwara ni ai tinda ina da ke kuma ansan dangin mahaifiyata...." Mommy jikinta ne yayi sanyi jin abunda Junaid ya faɗa, ɗagowa tayi tana kallonsa wanda shima kallonta yake, bata ankara ba taji ya sake jifanta da wata tambaya "shin su waye dangin mahaifina? sannan aina suke? meye asalinsu? duk bakisan wannan amsar ba, kawai kin Auri mutu bakisan ko shi wayene ba, baku tsaya kunyi bincike akansa ba, kunyi abunda yanzu nine nake jin zafinsa! kuma haka kikeso ki sake aikata kuskuren da kika aikata a baya? kina so na Auri wacce ba'a San asalinta ba, koda danginta baki saniba, kinaso na Aureta ƴaƴana suzo suna kukan gorin da ake musu cewar ba'a San asalin dangin mahaifin ubansu ba haka kuma ba'a San asalin dangin uwarsu ba, haka kenam zasu tashi da wannan takaicin? hatta ƴan uwanki ba sona sukeyi ba saboda basu san waye mahaifina ba, suma kansu ƴan uwanki gori suke mun balle azo cikin gari kan abokai da sauransu...." Mommy tana zaune kamar wanda ruwa ya cinye, bakinta har wani kakkarwa yake maganganun Junaid sun ƙona mata rai tace "Junaiddd ka dakata haka, duk da ba'a San ko waye mahaifinka ba amma shi ɗin mutumin kirki ne, yanada kyakkyawan zuciya wanda hakan yasa mahaifina ya damƙa masa amana ta saboda yasan zai kula dani, kuma Alhamdulillah tinda mukayi Aure har muka haifeka har mahaifinka yabar duniya bamu taɓa samun matsalar zamantakewar Aure ba, har yau ban taɓa yin danasanin Aurensa ba, hakan ma ka gode wa Allah tinda shi yayi sanadiyar zuwanka duniya, koda bashi na Auraba ba lalle ne kazo duniya ba saboda wani baya taɓa haifan ɗan wani, bazaka taɓa fitowa daga cikina ba saidai na haifi wani daban domin kai ɗin jinsin mahaifinka ne, saboda duk wanda yasan mahaifinka toh tabbas idan an ganka anga suffarsa...." Mommy ta ƙarasa maganar tana sharar hawaye, ta cigaba da cewa "Junaid bazaka taɓa tozarta ba a duniyan nan Insha Allahu koda bayan rai nane domin wannan dukiyar da muke sarrafa shi ya faro asaline daga mahaifina wato Alhaji Junaidu kafin rasuwarsa ya mallaka mun dukiyarsa da mahaifinka domin iya mu biyu kawai yake gani kuma ya yadda da mu duk da niɗin dole dukiyarsa nawa ne saboda ni kaɗai ya haifa, dukiyata dana mahaifinka amfanuwarka ne na kai ɗaya...." Junaid ne ya katseta da cewa "pleaseee Mommm it's okay ni ba maganar dukiya nake buƙatar ji ba, inason sanin su waye dangin mahaifina, daga wata ƙasar ya fito..." Mommy tace "Junaid abunda kake son sani nima ban saniba, abunda na sani akan mahaifinka shine mahaifina ya haɗu da mahaifinka ne a titi yana yawon neman aikinyi saboda abincin da zaici ma gagaransa yake, wata rana mahaifina yaje office ɗinsa dadaddare yana kan hanyar dawowa gida kwatsam saiga ɓarayi sun tareshi kuma alokacin yana tareda maƙudan kuɗaɗe na kamfani wanda zaiyi kimanin Billion 100 acikin akwati, ɓarayin nan sun so su illata mahaifina sannan su karɓe kuɗin sai Allah ya turo mahaifinka a yawace-yawacensa yazo wajen ganin abunda ake shirin aikatawa ne yasa yazo da gudu ya ceci mahaifina sannan yayiwa ɓarayinnan dukan gaske wanda har kasa tashi sukayi daga ƙarshe aka ɗauke su aka kaisu hannun hukuma, toh daga wannan lokacin ne mahaifinka ya shiga zuciyar mahaifina har ya ɗora shi akan kasuwancinsa, ansha tambayar asalinsa amma ya kasa gaya mana sakamakon ciwon mantau daya haɗu dashi duk ya manta daga inda ya fito, amma zubinshi ba ɗan Nigeria bane, irin bahindiyawan mutanen nan ne anfi tunanin daga ƙasar India yake, amma sai dai har yanzu ba'a gano ba har yabar duniya..." Junaid tsayawa kallon mommy yayi bayan ta kammala bashi labarin abunda ta sani ya turo ɗan ƙaramin bakinsa yace "Hmmm matsalar ƴan Nigeria kenam shikenam daga temakon da yayi muku sai kawai ki Aure shi?..." Mommy tashi tayi tana faɗin "your very stupid Junaid, bari naje kitchen domin nasan yunwa kake ji shiyasa ka kasa fahimta ta.." Har zata fita ta sake juyowa da sauri tace "Junaid bakayi sallar mangarib ba gashi har ana ƙiran Isha'i, why Junaid? please kaje masallaci banson sallarka a gida..." tana kaiwa nan tayi ficewarta... Shima tashi yayi ya nufi toilet zai ɗauro Alwala... Kitchen mommy ta shiga ta haɗa mana haɗaɗɗen girki! Abinci kala biyu ta girka kowa ta dafa masa abunda ransa yake so, Shi Junaid indai a night lunch ne yafi son sakwara da miyan ugusi da kifi haka Angel ma ra'ayinsu yazo iri ɗaya, Mommy kuma ita da Ayush sunfi son tuwon shinkafa da miyan ƙwai ko jar miya 😋😋😋😋😋 Junaid ne ya dawo daga masallaci zama yayi a falo yana kallon labarai, ta ko wani tasha labarin zuwa yaƙi ƙasar California ake, ana nuno photon Sarki Raamud a tv, sannan aka dawo nuno photunan sojojin da zasuje yaƙin! kowani ƙasa ana zaɓan sojojin da zasuje, Aka zo kan sojojin Austaraliya Junaid yana ganin yanda aka nuno photon Rumana, murmushi kawai yayi tareda girgiza kai shi inda ason ransa ne da baza'ayi yaƙin nan da mata ba, domin a tunaninsa mata babu abunda zasu iya sai shirme da kuma suzo suyita ihu a mutane, gani yayi anzo kan sojojin China, nan ma yaga an nuno photon Aditi dariya yayi a fili yace "gwara ke Sarkin faɗa..". Bayan su sai aka nuno sojojin ƙasan da za'ayi yaƙin wato California Army aciki har da Angel ɗinsa lokaci guda kuma sai yaji tausayinta duk da Angel commander ce amma bayaso a tafi yaƙin nan da ita domin ita ɗin tanada rauni sosai ba kamar su Aditi ba, Anan ana wuce ƙasashen sojojin da zasuje har aka zo kan ƴan Nigeria, tsuka Junaid yayi yana faɗin "Nigeria Army kam ba abunda zasu iya, ni ban taɓa ganin ragwayen sojoji irin na nan Nigeria ba wallahi, sai gadarar aita jefar da bindigu suna guduwa..." gani yayi an nuno photonsa ana sanar da cewa shine na ɗaya acikin jaruman sojojin Nigeria, tsuka yayi ya tashi yana faɗin "banson shirme, kuna wani ƙirana da jarumi wato so kuke azo mun ta baya a hallaka ni kenam..." yabar kallon ma ya nufi dinnig table sabo ƙar dashi saboda a yau ɗin nan aka kawo shi wancan table ɗin Junaid ya dagargaza shi... Zama yayi yana ƙiran Mommy tareda cewa "Ni har yanzu ba'a kammala girkin bane.." Mommy ce ta fito ɗauke da kulolin abinci ta jejjerasu, ɗagowa tayi tana kallon agogon ɗakin, da sauri tace "na shiga uku ina yaran nan suka shiga ne?.." Junaid yace "ina suka je ne?.." tace "wallahi ban saniba, tinda rana suka fita gashi yanzu har ƙarfe 10..." Junaid yana kallon kular abinci yace "Mom yunwa nake ji, ai ba ɓata zasuyi ba..." Mommy tace "Dan Allah Junaid kafin ka fara cin abincin kaje ka nemo su mana..." Junaid ya ɗago yana kallon Mommy tareda faɗin "whattt sorry I can't leave my food, ai su ba ƙananun yara bane da har sai an fita nemansu, idan sunada hankali ai da sukaga dare yayi sai su dawo gida..." Mommy tace "toh ai su basuda hankali sai an nemo su.." Junaid yace "toh su kwana acan indai ni zan nemo su.." Mommy zatayi magana kenam ya katseta da cewa "Please Mom am hungry, wallahi idan nabar abincin nan toh na basshi kenam zan kwana da yunwa ne..." Mommy tace "toh toh gashi ka fara cin abincin tukun saika je ka dubo mun su, idan ka gansu a hanya ka daka mun su..." ta ƙarasa maganar tareda zuba masa abincinsa a plate, yace "toh shikenam kije ɗakina ki buɗe wardrobe zakiga dorina ki ɗauko mun, yau zasu raina kansu tinda yawo zasu koya..." Mommy kallonsa take tace "toh bari na ɗauko.." a cikin ranta kuwa cewa tayi "tab wannan ai kaine sarki zalimun ɗin..." ta nufi upstairs tana takawa har ta iso ɗakinsa... Gari kuwa hadari ne ya haɗu sosai lokaci guda kuwa aka fara ruwan sama da ƙarfin gaske don ko yayyafi ba'ayi ba, irin ruwan nan mai haɗe da iska ake yi, Junaid yana cin abinci haka ya ƙara kallon agogo yanzu har 10:30 kuma ruwa ake sosai, ɗaukan wayansa yayi yana dialling call number Angel wayar ce take ringing har ta katse ba'a ɗauka ba, tsuka yayi ya ajiye wayarsa a gefen table har ya kammala cin abinci ya zauna kamar mai yin tunani... Mommy ce itama ta sauƙo down stairs hannunta riƙe da dorinar da Junaid yace ta ɗauko, tsayawa tayi ta jingina da jikin gini gaba ɗaya ta shiga damuwa, kallon yanda Junaid yake a zaune tayi tace "gashi anata ruwan sama kaima ba halin fita, na ƙira wayar Angel shuru bata ɗauka ba Allah dai yasa lafiya.." Junaid ne ya kalli Mommy yace "shine kika shiga damuwa haka?..." Junaid yana rufe baki sai suka ji an turo ƙofa da ƙarfi, da gudu Angel da Ayush suka shugo cikin falon duk sunyi jirib sai haki sukeyi kamar waɗanda sukayi gudun tsere... Mommy sake baki tayi tana kallonsu tama rasa bakin magana, shima Junaid kallonsu kawai yake yi, shine ma ya fara yin magana yace "daga ina kuke?.." Angel tana fitar da numfashi daƙer tace "wallahi motar mu ne ta ɓaci mana a hanya, tin daga teepa garage muke tafe da ƙafa har muka iso gida, babu abun hawa ko ɗaya..." Mommy tace "toh ina zakiga masu abun hawa acikin ruwan nan ga dare yayi yanzu sha ɗaya saura, na ƙira wayanki no picking kuma kafin ku fita saida na tambayeku ina zakuje baku gaya mun ba, wani irin hauka ne wannan..." Angel tace "Sorry Mom, munje gidan Malam Lawan ne.." Mommy tace "ai nayi waya da shi malam lawan bai ce mun kuna gidansa ba," Angel tace "wallahi Mom a gaban mu ai kukayi wayan naji kuna maganar ɗaurin Aure, toh Amma Mom ni Auren wa za'ayi?.." Mommy kawar da kanta gefe tayi tace "bansani ba kinyi laifi kuma kin saura da tambaya na abunda bai shafeki ba..." a ranta kuwa cewa take "kaji mun ƴar banzar yarinya zata tona mun asiri nida nake ɓoye maganar auren..." Ayush kuwa tin shugowarsu falon ta zauna a ƙasin carpet tana maida numfashi, domin ba ƙaramin gudu suka sha ba, gwara ita Angel ta saba da motsa jiki.. Junaid ne ya taso yana faɗin "Mom bani dorinan nan, jikinsu zai gaya musu ai..." Mommy har zata miƙa masa Angel tayi saurin fizgewa tana cewa "tabɗin jan ai wallahi impossible, haba Mom keda kanki zaki goyi bayan a daka mu kamar wasu karnuka tab.." Junaid ne yayo kanta yana faɗin "ki bani dorinar nace.." Angel tana turo baki tace "haba dai soja ce fa niɗin, har zan bari ana dukana kamar wata non living thing, duka ai saina yaƙi idan munje mu.." Junaid yana kallonta yace "Ni kike gayawa haka?..." ƙara turo baki tayi, hannu yasa ya jawo lips ɗinta yana faɗin "zan yanke bakin fah" Mommy kuwa nufo gurin Ayush tayi tana cewa "wannan ƙaton hijab ɗinki bazaki jiƙa mun carpet ba wallahi..." haka tasa hannu ta cirewa Ayush hijabin jikinta, ta buɗe ƙofa taje ta shanya shi ta dawo... Ayush kuwa da gudu ta tashi ta haura upstairs ta nufi ɗakinta saboda doguwar rigane a jikinta na bacci mai hannun breziya, Junaid tsayawa kallonta yayi har ta ɓace daga ganinsa, Mommy ce tace "wallahi Junaid kayi mata dukan tsiya indai bata faɗi abunda ya zaunar da su har wannan lokacin ba..." Angel tana turo baki tace "haba Mommy abun farin cikine ya samu fah.." Mommy tace "meye abun?.." tana dariya tace "Mom na musulunta dai" Junaid haɗe girarsa yayi cike da mamaki yake kallon Angel, Ita kuwa Mommy zaro ido tayi waje tace "Angel musulunta kuma? Aina?..." Angel tana kallonsu ɗaya bayan ɗaya tace "to kodai bakuyi murna ba?..." Mommy tace "bawai bamuyi murna ba, kawai dai unsuspecting..." Angel tace "wallahi tallahi Mommy wutar jahannama indai ƙarya nake..." Junaid jin kalar rantsuwar da Angel tayi yasa dariya ta kuɓuto masa, dariya ya shiga yi harda kama ciki, zaman yayi akan kujera yana dariya, daƙer ya iya dakatar da dariyar yana faɗin "wato yanzu kinsan wutar jahannama koh?.." Angel tana kallonsa tace "eh mana yanzu nasan wutan jahannama..." Mommy tace "toh banda abunki Angel ai saiki sanar mana koh, nima naso ace a gabana kika musulunta ai..." Angel tace "ai mommy munyi video lokacin da nake musulunta, Ayush ce ma take mana video na sanyawa kaina suna Maryam..." Mommy cike da farin ciki tace "kaiii amma naji daɗi wallahi, sannu maryamu..." Angel tana dariya tace "ai abunda yasa muka daɗe saboda an koyamun karatun Alkur'ani irin short short ɗin nan wanda zan rinƙa karanta su a cikin sallah amma saika fara karanta fatiha tukunna.." Mommy tayi hamdala cike da murna... Junaid yana kallon Angel cikin damuwa yace "wani irin ƙalubale zaki fuskanta idan har iyayenki suka ji kin musulunta? Kinsan mahaifinki tsohon soja ne hakan yasa ya ɗoraki akan aikinsa saboda iya ke kaɗai suka haifa, idan kuwa mahaifinki yaji toh acikin biyu ne za'ayi ɗaya! ko ya kashe kansa ko kuma ya kasheki domin babu abunda yafi tsana kamar musulunci ke kuma kinason mu'amala da musulmai gashi har takai kin musulunta, Angel mahaifiyarki zuciyarta zata iya bugawa saboda ita ɗin pastor ce a babban church ɗin ƙasar ku, toh mezai faru kenam?..." Hawaye ne suka fara gangaro mata tana sharar hawaye haɗe da murmushi tace "bazan sanar musu yanzu ba sai mun kammala yaƙin da zamuje, da zarar mun dawo zan ɗora video musuluntar danayi a social media kowa ya gani, duk hukuncin da iyayena suka yanke mun shikenam, idan ma kasheni za'ayi naji zan amshi hukuncin, idan kuma sune suka mutu zan nema musu gafarar Ubangiji, idan korana sukayi ai nan ma gidan mu ne, idan inaso nayi hutuna zan rinƙa zuwa nan Nigeria ina hutawa na..." Mommy tayi matuƙar tausaya mata itama saida ta zubda hawaye tace "Maryam kiyi haƙuri kinji koh babu wanda zai kashe ki, ni daman na ɗaukeki a matsayin ƴata wacce na haifeta a cikina, zaki zauna damu anan idan kuka kammala yaƙin ku domin ajiye aikin soja zakiyi saboda ki kare mutuncin kanki na ƴa mace, musulunci yanada ƙa'idoji da yawa, zan Aurar dake a duk wanda kike so...." Mommy taja dogon numfashi sannan ta kuma cewa "ni yanzu ma na rigada na yanke hukuncin zan haɗaki Aure da Junaid da zarar kun dawo..." jin haka saida ƙirjin Angel ta buga da ƙarfi, maganarta har yana harɗewa tace "Mom mom mommy Aure kuma da Ogah Junaid? to to Ayush fah?..." Mommy tace "duk ba damuwa zai haɗaku ku biyun..." Angel ta kalli Junaid yanata danna wayarsa shi ko alamar nuna damuwa baiyi ba tace "toh Mommy shi Ogah Junaid ɗin yanada ra'ayin hakan ne? baki tambayeshi ba.." Mommy ta kalli Junaid sannan tace "toh Ogah Junaid shin ka yadda zaka Auri Maryama?..." Murmushi Junaid yayi yace "duk abunda kika yanke Mom..." Angel dai har yanzu hankalinta bai kwanta ba saboda Ayush tace "Mom toh Ayush fah? bazata yadda da hakan ba, kuma inajin tausayinta...." kafin Angel ta rufe baki saiga Ayushert ta katseta da cewa "Aunty Angel ki daina sakani a lissafin ƴan matan Yaya Junaid, kedai idan zaki Aure shi ki Aureshi amma ni bana layin matan da yakeso, ni bazan taɓa Auransa ba, kuma bana ji araina zan Aureshi kuma shima haka, meyasa kuke son haɗa soyayyata da nashi alhalin bama son junan mu..." Mommy sake baki tayi tana kallon Ayush, acikin ranta take magana tace "mai wannan yarinyar take faɗane haka, bayan an rigada an ɗaura muku Auren..." Junaid shima kallon Ayush yake yana maganar zuci "nidai har cikin zuciyata ina matuƙar ƙaunarki Yushert, amma dole zan fitarki a zuciyata saboda zargin da nake miki na rashin gaskiya shin ke Aljana ce ko mutum?..." Ayush ce ta tsaya a gaban Angel tana goge mata hawayen da yake zubo mata tace "gaskiya na matsu sosai danaga ranar Auren nan! Aunty Maryam da Yaya Junaid Allah ya nuna mana lokacin, Allah ya sanya alkhairi..." ta ƙarasa maganar tana dariya ta juya da gudu ta koma ɗakinta, tana shiga ta rufe ɗakin ta faɗa saman gadonta, wani irin kuka ne ya zo mata, kuka take na gaske tana jin yanda soyayyar Junaid yake mata raɗaɗi acikin zuciyarta, tana faɗin "innalillahi wa inna ilaihi raju'un nashiga uku, soyayya zai mun illa, duk tsawon lokuta dana ɗau ina renon soyayya yanzu na tashi a tutar babu, Wallahi bazan iya haɗa soyayyata da wata ba, bazan iya juran ganin soyayyata tana hargutsuwa dana wata a zuciyan mutum ɗaya ba, wallahi na haƙura da Yaya Junaid, na haƙura wallahi! na haƙuraaa..." haka take ta rera kuka ita kaɗai a ɗaki... Itama Angel ɗakinta ta nufa da kuka tana shiga tasa sakata ta haura kan gado tana kuka da jiƙaƙun kayanta ko damar ciresu bata samuba, ita kukanta shine bata son Ayush da Junaid su rabu da juna, kullum yaƙinta shine ta shawo kayuwansu su zama masoyan asali lokaci guda kuma mommy ta tarwatsa komai.... Mommy tana tsaye akan Junaid tace "ni waɗannan yaran ban gane musu ba, ita Ayush ta tafi tana dariya ita kuma Angel ta tafi tana kuka..." Ajiyar zuciya Junaid yaja ya miƙe tsaye yana faɗin "ki rabu dasu Mom, kawai kije ki kwanta..." yana kaiwa nan ya haura upstairs, Ita kuma mommy wucewa ɗakinta tayi itama..... Toh nidai Abincin da aka bari a dinning table, gaskiya readers kuzo muje mu cinye kawai domin basa cin abincin daya kwana🙄🙄🙄 Haka kawai muna ji muna gani bazamu bari muga ana amobazanci da Abinci ba atoh😏😏😏😏😏😏 𝑡𝑦𝑝𝑖𝑛𝑔✍️ 𝗠𝗔𝗧𝗔𝗥 𝗗𝗔𝗠𝗨𝗦𝗔 the wife of a tiger🐅🐅🐅🐅 𝙼𝚊𝚕𝚕𝚊𝚔𝚒𝚗 𝙰𝚜𝚖𝚎𝚎𝚝𝚊𝚑 ✍️✍️ 𝙿𝚊𝚒𝚍 𝚋𝚘𝚘𝚔 𝚌𝚊𝚕𝚕 𝚘𝚛 𝚠𝚑𝚊𝚝𝚜𝙰𝚙𝚙 09065443871 *💫💫{{N W A}}💫💫* Book two C̶h̶a̶p̶t̶e̶r̶ 27 ➡️ 28 Ayush tashi tayi daga kwance ta shiga toilet domin watsa ruwa ajikinta.. Shima Junaid ɗakinsa ya shige kai tsaye toilet ya nufa ya watsa ruwa ajikinsa shaf-shaf sannan ya fito ya mulmulka cream ajikinsa mai ƙamshin gaske, ya nufi wardrobe ya zaro ƙananun kayansa three-quarter da t-shirt ya sanya su, zama yayi a bakin gadonsa yayi shuru kamar mai tunanin wani abu, lokaci guda ya miƙe tsaye ya wurga wayansa saman gadonsa ya fice a ɗakin... Ayush fitowa tayi tana ɗaure da towel a ƙirjinta zuwa gwigwarta bayan ta mulka cream a jikinta tsayawa tayi a gaban mirror tana kallon kanta, amma saidai da tunanin da takeyi, hawaye ne yaketa faman gangaro mata! tana cikin wannan tunanin taji an turo ƙofar ɗakinta ta cikin madubin ta hango wanda ya shugu ganin Junaid ne yasa ta juyo da sauri tana fuskantarsa, wani irin haɗiyar yawu ta yi! idonta ta kai kan agogon ɗakin taga ƙarfe 12 da mintina, Ƙarasowa gabanta yayi ya tsaya suna kallon juna yace "kina son tambayata meya kawo ni ɗakin ki a wannan daren koh?.." Ayush kallonsa kawai take ta rasa bakin magana, Shi kuwa sai ƙareta yake da kallo daga sama zuwa ƙasa, jikinta kamar ƴar bebin roba tsabar fari ga yanda yake ta sheƙi yana ɗaukan ido, hannu ya kai ya dafa kafaɗarta, a zabure Ayush taja da baya tana faɗin "ka daina taɓani saboda babu wata alaƙa da yake tsakanin mu.." kallonta yake cike da mamaki yace "idan kuma naƙi fah?..." Harararsa tayi sannan ta juyo zata nufi wardrobe ta ɗauki kayan da zata saka, hannu yakai ya riƙota tareda jawota jikinsa yana faɗin "Ni kike wa rashin kunya?..." ƙoƙarin barin jikinsa takeyi shi kuwa ya riƙeta sosai, kokuwa suka shiga yi yana faɗin "kika ce bakya sona koh? meyasa kika ce haka?.." Kuka ta fara yi tana cewa "ka sakeni ni, wallahi bana sonka ka sakeniii..." daƙer ta zame masa da gudun gaske ta juya zata gudu ƙafarta ya harɗe zata faɗi ƙasi yayi saurin riƙota, shima ruɗewar da yayine yasa suka faɗi a saman gado gaba ɗayansu... tinda Junaid ya faɗa saman Ayush yayi shuru bai ƙara motsawa ba, gaba ɗaya ƙamshin jikinta duk ya kashe masa jiki, haka itama daga lokacin bata ƙara motsawa ba, gaba ɗayansu kamar wanda ruwa ya cinyesu, saida suka ɗau lokuta basu motsa ba, sai bayan nan Ayush ta ɗan motsa tana ƙoƙarin tashi, Junaid ya ƙara matseta ya kai fuskarsa saitin nata haka numfashinsu yake gaurayuwa, gaba ɗaya Junaid ya fita hayyacinsa haka ya fara kissing ɗin wuyanta zuwa saman lips ɗinta yana shafa sumar kanta, Ayush kam tana jinsa amma ta kasa dakatar dashi tayi shuru itama tana shirin fita hayyacinta,. Junaid ne ya kama lips ɗinta yana socking kamar yaron da yake shan nono, ganin bazata iya shuru ba haka itama ta fara maida masa da martani, lokaci guda taji wani irin tsananin ƙaunarsa ya mamaye mata zuciya, rungumarsa tayi sosai tana sumbatu tareda kama harshensa tana tsotsa cikin salo, topah Ogah Junaid an daɗe ba'a haɗu ba, gaba ɗaya ba ƙaramin rikicewa yayi ba, ya ƙanƙameta sosai gaba ɗaya duk ya hargutsa mata sumar kanta, cikin ƙanƙanin lokaci duk ɗinsu suka ɗauke wuta, sun daɗe suna romance daga baya Junaid yaja musu mayafi, duk ba wanda hankalinsa yake jikinsa, Bayan ɗan mintuna kaɗan sai mukaji ihun Ayush! wani irin gigitaccen ƙara tayi lokaci guda kuma tayi shuru sai faman shure-shure take tana kuka ciki-ciki domin kukan ba wani jinsa ake sosai ba, sai yakushin Junaid take a baya tana faɗin "nashiga uku ka kyaleni zan mutu dan Allah, ka tausaya mun wayyo da zafi wallahi! Yaya Junaid ka barni haka da ciwooo...." ta ƙarasa maganar tana sheshsheƙar kuka.. Shi kuwa Junaid sai faman aiki yake domin duk abunda Ayush take faɗi ba jinta yake yi ba, gaba ɗaya kunnuwansa sun toshe baya jin komai sai faman gurnani yake yana nishi sama-sama kamar wanda numfashinsa zai ɗage, ya shiga duniyarda tinda yake bai taɓa shiga ba, yanayin da ya shiga yafi ƙarfin ƙwaƙwalwarsa, yana cikin wannan yanayin kwatsam numfashinsa ya ɗage, lokaci guda ya daina motsi sakamakon sumar da yayi, Ayush ganin nauyin yayi yawa kuma gashi baya motsi ga raɗaɗin da take ji a ƙarƙashinta haka tasa hannu ta tureshi da ƙarfinta, mirginawa yayi gefe guda, Ayush numfashi take fitar wa sosai still tana kwance ta gagara tashi, jikinta duk yayi nauyi, ga Junaid a gefe guda yana sume... Ayush ganin Junaid baya motsi a tunaninta bacci yake yi, haka take ƙoƙarin tashi daƙer domin ba ƙaramin zafi farjinta yake mata ba, yaye mayafin gadon tayi daga kanta abunda ta ganine ya ruɗar da ita cikin firgici ta buɗe baki ta zabga uwar ihu tana zazzaro ido waje, Jini ta gani duk ya malale gadon kuma daga jikinta, abun ya bata tsoro matuƙa, tana cikin wannan firgicin kawai taji ana buga ƙofar ɗakin tareda faɗin "Ayush lafiyanki kuwa, meya sameki kike ta faman ihu?..." cikin tsoro murya a harharɗe Ayush tace "Mo mo mommy babu komai! Ma ma ma mafarki nayi..." Mommy tace "toh da farko naji ihunki nayi tunanin mafarkin ne, kuma du yanzu na sake jin ihunki ba sau ɗayaba, ki rinƙayin addu'a idan zaki kwanta..." Murya a shaƙe Ayush tace "toooh..." cikin yanayin kuka, Mommy tace "toh karfa ki koma bacci saboda yanzu an kusan ƙiran sallar asuba, ki tashi kiyi sallar lafula..." tana kaiwa ƙarshe tabar jikin ƙofa ta sauƙa down stairs ta koma ɗakinta.." Ayush kasa motsawa tayi tana kallon shimfiɗar data ɓata da jini lokaci guda kuwa ta fashe da matsanancin kuka tana dafe da goshinta, Sai a lokacin tayi nadamar biyewa Junaid, ƙololuwar baƙin cikine ya isheta, tanata rera kuka, ji take kamar ta rufa Junaid da duka "abun baƙin ciki ya rabani da budurci na, ya rabani da mutuncina wayyo kaico.." juyowa tayi tana kallon Junaid cikin ɓacin rai lokaci guda kuma ta dakatar da yin kukan tana kallon bayansa duk ta jimasa ciwo tsabar yakushin da tayi masa, kawar da kanta tayi gefe tana ƙoƙarin tashi daƙer ta iya sauƙa daga kan gadon tana ɗingishi daƙer take iya tafiya ta nufi toilet, can sai gata ta fito hannunta riƙe da bucket na ruwan zafi ta ajiye bucket a ƙasin gado sannan ta ɗauko ɗan ƙaramin mayafinta tasa a cikin bucket ta tsame mayafin a cikin ruwan zafi tana ƙonewa da haka ta hau saman gadonta ta fara dannewa Junaid bayansa da ruwan tana ɗumama masa bayan, haka take wannan zirga-zirgar sauƙowa a gadon ta jiƙa mayafin ta hau ta ɗumama masa jiki da haka har ya farfaɗo, idonsa kawai ya buɗe yana lumshesu a hankali, jin yanda Ayush take ɗumama masa jiki yasa shi sauƙar da ajiyar zuciya yana jin daɗin matsar da take yi masa, juyowa yayi da murmushi a fuskarsa, ya ƙara haske sosai fuskar yayi fiyau kamar wanda yayi rashin lafiya, daƙer ya tashi zaune yana kallon Ayush, wacce itama tana zaune ta zuba masa ido cikin ɓacin rai ko Annuri babu a fuskarta, juyawa tayi ta sauƙa daga saman gadon ta ɗauki bucket ɗin ta nufi toilet, Junaid ganin yanda Ayush take ɗingishi sosai yasa shi zabura ya zaro ido waje yana kallonta, shi duk bai lura da gadon data ɓata da jini ba, sai a lokacin ya sauƙar da idonsa kan mayafin gadon duk a ɓace da jini a hankali ya furta "Innalillahi wa inna ilaihi raju'un, mena aikata haka?..." Da sauri ya sauƙa daga kan gadon shima ya nufi toilet, yana shiga ya tarar da Ayush tsaye a gaban madubin toilet tana ta faman rera kuka..." zuwa gabanta yayi dasauri cikin nuna damuwa yace "Yushert dan Allah kiyi haƙuri, banyi miki haka dan na wulaƙantaki ba, ki gafarceni dan Allah..." Itama juyowa tayi tana fuskantarsa cikin kuka take faɗin "Yaya Junaid ba abunda zanje maka sai dai Allah ya isana tsakanina da kai, ka tozartani sannan ka cuceni, ka zubar mun da mutuncina ka kawar mun da budurci na, toh daman ƙiyayyata har takai haka a cikin zuciyarka? Yaya Junaid shin laifin dana aikata maka har na cancanci wannan hukunci? wallahi naji na tsaneka wallahi na tsaneka bana ƙaunarka bana ƙaunar mai irin halayenka...." lokaci guda ta fashe da kuka, Junaid sam baiji daɗin kalamanta ba haka ya jure ya riƙo hannayenta biyu yace "Yushert meyasa kika amince dani? meyasa a lokacin bakiyi ihu a kawo miki agaji ba? Yushert ki sani har yanzu ina sonki kuma bazan daina sonki ba har abada, koda da lokaci ɗaya ban taɓa tsanarki a cikin zuciyata ba..." a fusace Ayush ta fizge hannunta daga cikin nashi tana faɗin "Ni na tsaneka wallahi, ka shugo mun ɗaki ka keta mun haddi, wallahi sai Allah yabi mun hakkina, azzalumi kawai macuci..." tana kaiwa nan ta ratsa ta gefensa zata fita kawai taji jini ya yanko mata, tsayawa tayi takai idonta saitin ƙafafunta taga yanda jini yake bin ƙafarta yana zuba, tsorone da firgici ya kamata! buɗe baki tayi zata kurma ihu Junaid yayi saurin toshe mata baki da hannunsa lokaci guda kuwa ta faɗa jikinsa take numfashinta ya tsaya cak ta sume a jikinsa, Idon Junaid ne yayi jawur kamar zaiyi kuka haka ya ɗauki Ayushert ya ajiye ta a cikin bahon wanka tareda zamar mata da towel data ɗaura dake shiɗin bai ɓaci da jini ba, fanfo ya kunna mata na ruwan zafi, ya barta a ciki ya fice da sauri ya koma bedroom yaje ya yaye mayafin gadon ya gyaggyara gadon sannan ya shimfiɗa sabon zanin gado, ya gyara mata ɗakin gaba ɗaya, ji yayi anata ƙiraye-ƙirayen sallar asuba anan hankalinshi ya ƙara tashi domin yasan dole Mommy zata zo tashin Ayush yin Sallah, kuma zataje ɗakinsa! komawa yayi cikin toilet a ruɗe da zanin gadon daya ɓaci haka yasa a bucket ya zazzagi omo ya fara wanke zanin gadon, shi tinda yake ma bai taɓa yin wanki bama sai yau... Ita kuwa Ayush jin yanda ruwan zafi yake ratsata ne yasa ta farfaɗo tana cikin baho ko kallon yanda Junaid yake batayi ba sai hawayen da yake gangaro mata, tayi shuru ko motsi batayi sai faman lumshe ido take... Junaid da iya ƙarfinsa ya wanke bedsheet ɗin nan tas ya shanya shi acikin toilet ɗin dake akwai igiyar shanya a ciki, yana gamawa da wannan ya nufi gurin Ayush, haka yasa hannu yana watsa mata ruwan ɗumi ajiki, itama saida ya wanketa tas ya ɗumama mata ƙasinta da hot water sannan ya ɗaura mata new towel daya ɗauko a cikin wardrobe ɗinta ya ɗauketa a saman kafaɗarsa suka fita bedroom, Duk abubuwan da yakeyi tana jinsa bata ce masa komai ba, tsananin kunya ne ya isheta shiyasa ta kasa motsawa domin duk ya kalle mata tsaraicinta, gaba ɗaya taji Junaid ya wanke mata a rai... Bugun ƙofa sukaji a yayin da Junaid ya zaunar da ita akan gadon daya gyara, Zuciyarsa ne ta fara bugun uku-uku, jin yanda aketa buga ƙofar ɗakin, muryar Mommy yaji tana ƙiran sunan Ayush akan tayi sallah ne ko kuwa, Junaid da sauri ya buɗe wardrobe ya zaro mata doguwar riga marar nauyi mai gajeren hannu yazo ya sanya mata shi, jin muryar Mommy ya kuma ji tana cewa "wai ni Ayush ƙalau kike ne? inata ƙiranki shuru kardai ace kin koma bacci ne, shin kinyi sallah ne ko kuwa?..." Junaid jin Mommy taƙi daina surutu kuma ga Ayush taƙi yin magana yasa shi yin muryar mata cikin sassanyar murya yace "ehhh nayiii....". yayi kalar muryar Ayush. Mommy tace "ok ai sai kiyi magana tin ɗazu..." tana kaiwa nan ta juya abunta, tana barin bakin ƙofar Ayush kai tsaye ɗakin Junaid ta nufa, Junaid yana jin yanda Mommy take bubbuga masa ƙofa tana ƙiran sunansa, Junaid dafa goshinsa yayi yace "oohhh mom kin cika damuwa.." Ayush kallonsa kawai takeyi babu alamun dariya a fuskarta, sunkuyawa yayi a gabanta yana dafe da cinyarta yace "Yushert ba roƙonki zanyi akan ki yafe mun ba amma kuma ina neman alfurmanki dan Allah, ki temakeni kar wanda yasan abunda ya shiga tsakanin mu, kar ki gaya wa mommy abunda na aikata miki Please ki temakeni Yushert..." Ayush tana sharar hawaye tace "ka tashi ka bar mun ɗakina, bana buƙatar ganin fuskarka dan Allah, ka temakeni ka bar mun ɗakina idan kuma yin fyaɗen Bai isheka ba ga fili ga Mai doki..." Junaid dafe goshinsa yayi yana faɗin "ohhhh my God! Yushert ki sani fah bawai fyaɗe nayi miki ba, wallahi bansan nayi miki haka ba, ba'a cikin hayyacina nake ba ki yadda dani manaa..." Ayush a fusace ta miƙe tsaye tana faɗin "i said leave my room, please stay away from me..." Junaid miƙewa yayi yana cewa "Okay okay it's okay, zan tafi yanzu ki kwantar da hankalinki..." yana kaiwa nan ya nufi bakin ƙofa zai fice, ganin Mommy ta fito a ɗakinsa ne yasa ya laɓe, Mommy kuwa a tunaninta Junaid har ya tafi masallaci ne, sauƙa down tayi... tana tafiya Junaid ya fito da sauri ya wuce ɗakinsa, zuwa yayi ya shiga toilet ya yi wanka da alwala ya fito yayi sallah ko masallaci baije ba a ɗakinsa ya yi sallar... Angel itama tana cikin ɗakinta tayi sallah abunta tana zaune akan sallaya duk fuska yayi jawur, ido yayi lufu-lufu taji wayarta yana ringing, tashi tayi a kasalance ta ɗauki wayar a saman gadonta tayi picking tareda karawa a kunne tana faɗin "Hello gud morning sir..." Sanar mata akayi cewa yau ne tafiyarsu ƙasar California tareda sojojin Nigeria domin yin shirye-shirye, gobe za'a fara gudanar da yaƙi, haka ko wace ƙasa sojojinta zasu tafi California ne..." Angel amsawa tayi da "Okay sir..." daganan aka katse wayar tana sauƙar da ajiyar zuciya saiga wani ƙiran ya sake shugowa ɗagawa tayi tana cewa "hello marshal sadeek well done.." daga ɓangarensa kuwa cewa yayi "yauwa commander Angel the Army of California how is day?..." amsa masa tayi cikin farin ciki, sannan yace "na ƙira wayan Captain Junaid tin cikin dare bai ɗauka ba, lafiya kuwa?..." Angel tace "ayya Ina tunanin bacci yake yi, amma ai maganar bazai wuce akan yau ne tafiya can ƙasar yaƙin ba koh?..." yace "of course, zan tunatar dashi ne akan yanzu haka ma an tanadar mana da jirgayen da zasu ɗauke mu, duk sojojin da za'a tafi dasu duk sun hallara sauran 1hour mu tafi, kuyi sauri Please..." Angel tace "innalillahi da wuri haka? toh yanzu ma zan sameshi muyi sauri mu shirya kam..." yace "Ok...". daganan suka katse ƙiran... Angel da gudu ta fice a ɗakinta kai tsaye upstairs ta haura tana zuwa ta shige ɗakin Junaid ta sameshi akan sallaya yana waya, ji tayi yana cewa "Okay Sir gamu nan fitowa.." katse wayar yayi ya miƙe tsaye yana kallon Angel yace "lafiya kuwa?.." tace. "daman nazo sanar maka..." bata ƙarasa maganar ba ya katseta da cewa "kije kiyi wanka don ni yanzu kayana kawai zan haɗa na rigada nayi wanka nah..." Juyawa tayi da gudu ta koma ɗakinta kai tsaye toilet ta shiga domin watsa ruwa... Bayan awa ɗaya Mommy ta kammala haɗa kayan breakfast akan dinning table, tana zaune a falon tana jiran fitowar su suzo suyi kumallo... tana zaune sai gani tayi Junaid ya sauƙo down yana jan akwatin kayansa yana sanye da kayan soja, (wayyo Allah ni tinda nake ban taɓa ganin Junaid a cikin kayan sojoji ba sai yau, kunga yanda yayi matuƙar kyau kuwa...) Mommy miƙewa tayi tsaye tana faɗin "lafiya kuwa naga ka fito da akwati Ina zakaje?..." Murmushi yayi sannan yace "Mom anyi mana ƙiran bazata yau ne tashin jirgin mu, kuma yanzu haka ma jiran mu akeyi jirgi zai tashi..." zuciyar Mommy ce ta fara bugawa da ƙarfin gaske tace "yau ne tafiyarku?..." lokaci guda kuwa ta fashe da kuka, Junaid ne yazo gaban Mommy ya rungumeta yana rarrashinta tareda cewa "kar ki damu Mom insha Allahu zamu dawo lafiya, kedai ki taya mu da addu'a duk da nasan dole wasu daga cikin mu zasu rasa rayukansu..." Mommy tana cikin kuka saiga Angel itama ta fito da akwatinta tana sanye da kayan sojoji na ƙasar California bana nan Nigeria ba, Itama zuwa gurin Mommy tayi tana rarrashinta, Mommy tace "toh amma zaku tsaya kuci abinci ai koh?..." Junaid yace "indai haka shi zaisa kiyi farin ciki toh zamu ci duk da mun makara..." Mommy tace "toh kuzo na baku abinci da hannuna kafin ku tafi..." wajen dinnig suka nufa haka mommy take ta feeding ɗinsu da hannunta take ɗiban abinci tana basu a baki, idan ta bawa Junaid saita juya tana bawa Angel da haka har suka ƙoshi... miƙewa sukayi kowa ya ɗauki akwatinsa suka nufi waje, mommy tana biye dasu tana ta musu addu'a da fatan cin nasara, Bayan sun isa wajen da motocin gidan suke haka Junaid ya buɗe bayan mota ya ajiye musu akwatinansu sannan ya rufe, ya juyo yana kallon Mommy yace "Mom zan aiko yarona ya kawo motar..." Mommy tace "a'ah My son ni zan rakaku har wajen jirgin da motar..." Junaid yace "toh mom ai headquarter zamuje daga nan acan zamu shiga jirgin.." Mommy tace "hauka nake bazan ga tafiyarku ba? zan kaiku har headquarters ɗin..." yace "toh Mom zomu tafi.." Mommy tace "Amma kunyi sallama da Ayush kuwa?..." bata rufe bakinta ba saiga Ayush ta fito tana ɗingishi haka ta ƙaraso wajen nasun... Angel kallo ɗaya tayiwa Ayush tasan akwai matsala, dole akwai abunda ya faru a tsakanin Ayush da Junaid a daren jiya" haka Angel take wannan tunanin a ranta... Mommy tace "lafiya kuwa Ayush yanaga kina ɗingishi?..." zuciyar Junaid ne ya fara bugawa da ƙarfin gaske gaba ɗaya ya fita hayyacinsa tsabar tsananin tsoro, haka yake bin Ayush da kallo..." Angel kallonsu take tana murmushi idan ta kalli Ayush saita juya ta kalli Junaid, cikin ƙanƙanin lokaci har ta karanci abunda yake cikin zuciyoyinsu... Murmushi Ayush tayi tana kallon Mommy tace "wallahi Mom Ina sauri zan sauƙo daga stairs kawai na zamo na faɗo akan gwiwata, shiyasa ƙafar ta riƙe mun..." Mommy tace "Ayya ki rinƙa tafiya a hankali mana, gashi kinji ciwo..." sunkuyar da kai Ayush tayi hawaye yana shirin ƙwato mata tayi saurin goge ƙwallar ta ɗago tana murmushi, Angel bata san lokacin da dariya ya kuɓuto mata ba jin rainin wayo irin na Ayush, taɓe baki tayi tana kallonta cike da mamaki... Ayush kuwa gaban Junaid taje ta tsaya suna fuskantar juna, ba Annuri a fuskarta haka ta ɗago da wani jan ƙyalle ta naɗa shi ta ɗaura akan goshin Junaid, sai ƙyallen ya ƙara haskashi kyanshi ya ƙara fitowa, Bakinta takai saitin fuskarsa ta sumbace shi a hankali ta furta cewa "inaso ka sani bazan taɓa sonka ba, i hate you! ka kula mun da kanka, Allah ya dawo daku lafiya kuma ka kula mun da wannan jan ƙyallen domin shine amanata, idan har ka ɓatar mun dashi to nasan babu amanar soyayya a tsakanin mu..." Mommy da Angel tsayawa sukayi suna kallon ikon Allah, Ayush nufan gurin da Angel take tayi tana zuwa ta rungumeta tana faɗin "zanyi missing ɗinki Aunty Maryam, Allah ya dawo mana daku gida lafiya musha biki..." Ayush tana kaiwa nan ta juya tana ƙoƙarin matse hawayen daya zubo mata, Mommy tace "Ayush kizo mu rakasu mana.." Ayush tace "a'ah bana jin daɗin jikina.." haka ta shige falo tana ɗingishin... Su Mommy kuwa mota suka shige, Junaid shine mai driving har suka bar harabar gidan still da wannan jan ƙyalle a goshinsa wanda Ayush ta ɗaura masa.... 𝑡𝑦𝑝𝑖𝑛𝑔✍️ 𝗠𝗔𝗧𝗔𝗥 𝗗𝗔𝗠𝗨𝗦𝗔 the wife of a tiger🐅🐅🐅🐅 𝙼𝚊𝚕𝚕𝚊𝚔𝚒𝚗 𝙰𝚜𝚖𝚎𝚎𝚝𝚊𝚑 ✍️✍️ 𝙿𝚊𝚒𝚍 𝚋𝚘𝚘𝚔 𝚌𝚊𝚕𝚕 𝚘𝚛 𝚠𝚑𝚊𝚝𝚜𝙰𝚙𝚙 09065443871 *💫💫{{N W A}}💫💫* Book two C̶h̶a̶p̶t̶e̶r̶ 29 ➡️ 30 Da gudu ta nufi toilet tana kwarara amai acikin sink, ƙarar aman da takeyi ne yajawo hankalin Ammy zuwa ɗakin da take, kai tsaye toilet Ammy ta shige ta tarar da Maimoon a sunkuye sai faman shiɗewa takeyi, Bayan ta kammala ne ta wanke bakinta sannan ta ɗago zata fice taga Ammy tana tsaye a bakin ƙofar toilet, Ammy kallon Maimoon take sosai cike da mamaki tace "Maimoon wai meyake faruwa dake ne kam? duk abunda kika ci saikin amar idan bakida lafiya ai saiki sanar koh..." Maimoon kanta a sunkuye tace "Ammy babu komai dai just tsutsar ciki ke damuna shiyasa duk abunda naci saina amar dashi..." Ammy tace "toh kizo na kaiki hospital, inyaso sai likita ya ɗauraki akan magani, Maimoon tace "a'ah Ammy ki barshi ba wani abu bane, tashin zuciya ne da zarar naci goro shikenam zai daina mun..." Ammy tace "toh shikenam Maimoon gaba ɗaya naga kin canza ne bakya son shiga cikin mutane why? kinbi kin rarrame kin tuttuje daga kuka sai kuka idan akwai wani abu ki sanar mun mana.." Girgiza kai Maimoon tayi tareda faɗin "don't worry your self my Ammy, komai lfy lau just yanayin ne yazo mun da haka, amma nasan abunda nake yi.." Ammy tace "toh shikenam Allah yasa.." daga nan tayi ficewar ta. Ita kuma Maimoon kwanciya tayi akan saman gadonta tana ta fatan sharar kuka... Ita abunda yake bata tsoro shine yau wata biyu da dawowarta gida amma bataga period ɗinta ba, kuma tin a gidan su Laylah ma ta daina ganin period ɗinta tsawon wata biyu agidan su Laylah, abun yana damunta saidai bata san ko meye matsalar ba.. ****** Ayush bayan ta shiga ɗakinta kai tsaye toilet ta nufa ta tsaya a gaban mirror tana kuka tareda faɗin "Umma! Umma ki fito mana, meyasa bana ganinku a cikin madubi yanzun, dan Allah ki fito akwai mayaƙan da suke son ganin bayanku, ku gudu, ku gudu dan Allah banaso na rasa ku, ina Narasimha kuce ya ɗauke ku....." Fashewa tayi da wani matsanancin kuka har saida ta durƙusa da gwiwowinta.. Bayan su Mommy sun isa headquarters itama kukan take sosai na tafiyarsu Junaid, Angel itama kukan take saboda basu san mai zasu tarar ba agurin yaƙin, Junaid ganin yanda Mommy taketa kuka yasa jikinsa yayi sanyi, murya a sanyaya yace "Please Mom ki koma gida zamuyi waya..." Daƙer Junaid ya rarrashi Mommy ta hau mota ta koma gida. Duk sojojin da za'a tafi dasu sun shishshirya kowa yana ɗauke da jakarsa na kakin soja, jirgi biyu ne suka tashi, jirgi na farko ya daɗe da tashi tin kafin su Junaid su iso, suma yanzu jirginsu ya tashi... Mommy tana komawa gida itama ta nufi ɗakinta ta kifu akan gadonta tana kuka tareda addu'ar Allah ya dawo mata da ƴaƴanta gida lafiya, Ayush ce ta sauƙo daga upstair tayi wankan ta cikin doguwar riga na material idonta yayi lufu-lufu ya kumbura tsabar kukan da tayi, waran dinning table taje ta zauna ta buɗe kula ta zuba abinci a plate don saida ta totsa plate ɗin da abincin tukun ta fara tura shi daman ba ƙaramin yunwa take ji ba, *BAYAN WASU AWANNI JIRGIN SU JUNAID YA ISA ƘASAR CALIFORNIA...* an tanadar musu da wani makeken hotel wanda zai iya ɗaukar duk sojojin da suka zo, sun ci sun sha saida suka ƙoshi tukun kowa yaje ya kama ɗakinsa, Ita dai Angel ta tanadar musu da ɗaki ɗaya ita da Junaid, kafin a tafi yaƙin, Misalin ƙarfe 12 na dare Junaid yana kan wata doguwar kujerar ɗakin yana ta faman danne dannen computer, ita kuma Angel tana kwance akan gado tana karatun littafi na English, babu wanda ya kula kowa a ciki sai sukaji ana Knocking Angel ce tace "waye ne?..." daga waje aka bada amsa cewa "serjan Umar ne nazo gurin Ogah Junaid.." Angel tace "toh coming..". buɗe ƙofar ɗakin akayi ya shigo da murmushi a fuskarsa ya nufi gurin Junaid yana faɗin "Ogah ga ƙaramin gun ɗinka ka manta dashi..." ya miƙa masa sannan ya juya yayi ficewarsa, Angel ce ta ciro bread da bota a cikin jakarta tace "My man sauƙo muyi kumallo amadadin abun ƙaryawar safe.. Junaid ne ya kalli agogo yaga ƙarfe 12 da rabi yace "Ni ba abunda zan ci yanzu, ki ci abincinki.." Tace "amma kasan da asuba zamu fita yaƙi koh? ba lokacin cin abinci, ka daure kaci dan Allah..." cigaba yayi da danna computer ba tareda ya ce komai ba, ita kuwa sauƙowa tayi ta fara cin abincin ta cikin nutsuwa, lokaci guda kuwa sukaji an turo ƙofa da ƙarfin gaske saida Angel ta tsorata, shima Junaid ɗagowa yayi yana kallon bakin ƙofa fuska a haɗe, tsuka yayi ya girgiza kansa tareda faɗin "ai daman nasan ba wanda zaiyi wannan aikin sai ke..." ya ƙarasa maganar yana danna computer sa... Aditi ce ta shugo a hanzarce tace "daman anan kuka fake, tinda na iso nake ta nemanka" ta juyo tana kallon Angel cikin fushi tace "ke kuma sarkin son maza kun zauna ɗaki ɗaya kamar miji ki mtts..." Angel tana zaune tana cin abincin ta ko kulata batayi ba, acikin ranta tace "oh wannan bazata taɓa canzawa ba.." surutun Aditi duk ya ishesu Junaid ne ya miƙe tsaye yana faɗin "meye matsalar ki ne Adity?..." Adity tana huci tace "bazaka kwana da mace a ɗaki ɗaya ba..." Yace "kina tunanin wani abu zai faru ne?.." tace "eh zata koya maka kwartonci ne, nidai nasan Ogah na ba ƙwarto bane, amma naga sai shishshige maka take tayi..." Angel ta tashi itama a fusace tace "wacece kwartuwa? ki shiga hankalinki wallahi..." kafin Angel ta rufe baki Aditi takai hannu ta naushe mata baki! Adity tana zaro ido tace "bana juran raini..." Angel hannu biyu tasa ta toshe bakinta wanda tunin har ya fashe, Junaid yace "Adity meyasa baza kiyi hankali ba? ku daina wannan shirmen kamata yayi kuje kuyita addu'a akan yaƙin nan gobe da asuba mah mun rigada mun tafi..." Junaid bai ƙarasa maganarsa ba itama Angel ta kawo hannu ta zabga mata mari a fuska nan suka kaure da kokuwa, Junaid tsuka yaja yabi ta gefensu ya fice a ɗakin kai tsaye ɗakin wani Abokinsa ya nufa yana zuwa kuwa ya shige .. Angel da Adity faɗa suke yi sosai gaba ɗaya sunyi kaca-kaca da ɗakin saida sukayi mai isar su tukun suka rabu, Amma saidai Angel tafi jin jiki domin ita Adity naushi kawai take yi, Adity tashi tayi tana zage-zage ta fice a ɗakin, Angel kuwa kanta a kife ta gagara ɗagowa ma, sai can bayan fitar Aditi itama ta tashi daƙer ta shige toilet tayi wanka sannan ta ɗauro alwala tazo tayi sallah tareda addu'o'i tana zaune akan sallaya bata rintsa ba har asuba ta tashi tayi sallar asuba sannan ta miƙe ta shirya cikin kayan sojoji saida ta shirya tsab sannan ta ɗauki bindigarta ta fice a ɗakin tana mai fushi da Junaid akan ya barta yayi tafiyarsa, tana maganar zuci tace "mutumin da bai damu dani ba, a haka Mommy take cewa zata haɗa mu Aure, yanzu inda Ayush ce bazai barta tayi faɗa da wata ba har aji mata rauni...." ta ƙarasa maganar tana sharar hawaye da haka har ta fita filin da zasu taru, duk safikonta saida ta samu sojoji da damarsu sun fiffito suma kowa yana riƙe da bindigunsa, Bayan minti talatin saiga Ogah Junaid shima ya fito cikin kakin soja yana rataye da wata ƙatuwar bindiga shima layi ya shiga domin kafin a tafi sai anyi wasu jawabai, yana tsaye saiga Ogah Rumana tazo gabansa itama cikin kayan soja tana mai farin cikin ganinsa shima murmushi yakeyi suka gaggaisa daga baya ta koma gurin tsayuwarta, saiga Adity itama tazo tana faɗin "waini wannan jan ƙyallen goshinka na meye ne? ko asiri kayi ne na yaƙar matsafi?.. " kallonta yayi sannan ya kawar da kansa gefe yace "ni ai babu ruwana dake tinda bakya jin magana..." Ogan su Adity ne ya daka mata tsawa akan ta koma gurin tsayuwarta, turo baki tayi ta koma, Angel kuma duk abunda sukeyi akan idonta ne ita kaɗai sai fushi take tayi, tayi alkawarin bazata kula Junaid ba har su kammala yaƙin su... ***** Sarki Raamud gaba ɗaya hankalin shi a tashe yake yanda Munafurr ya kullesu a ɗaki, Uma Bara'at ba abunda take sai kuka, suna zaune akan gado tace "dan Allah Sarki ka nema mana mafita, na gaji da zaman kaɗaici, ka duba mana ɓoyayyar hanyar da zamu gudu dan Allah..." Sarki Raamud yayi ajiyar zuciya sannan yace "kiyi haƙuri mu cigaba da zama har Allah ya kawo mana ɗauki, yanzu idan mukace zamu gudu Munafurr bazai barmu ba saboda yana kallon mu kinsan shi yana aiki da tsafi ne! kuma Damusa yana can a ɓoye guri guda fatana kar munafurr yasan da zaman Damusa Sujjur domin bazai barshi da rai ba, banaso na gudu nabar Damusa..." tana kuka tace "bamuda mafita kenam?.." yace "babu mafita sai abun da Allah ya tsara mana..." Uma Bara'at gaba ɗaya ta zamo kalar tausayi ta kwanta akan cinyarsa, shima rarrashinta yake yana bata baki tareda kwantar mata da hankali, ga cikin twins a jikinta har ya girma domin cikin bazai wuce 7month ba... Ta Ɓangaren Munafurr kuma sai zabga uwar dariya yake ganin yanda aka haɗa rundunar sojoji ta cikin madubi yake kallonsu, su sojoji tunaninsu shine zasu tarar da sarki Raamud ne, Munafurr magana yake a tsawace yana faɗin "bazaku iya baaa, bazaku iya dani baa, nafi ƙarfinku ƙananun ƙwari Hhhhh..." Shi Munafurr ko damuwa da zuwan sojojin nan baiyi ba saboda murƙusa ɗaya kawai zaiyi musu ya gama da rayuwarsu... Zaman sarauta yayi sannan ya tura macijensa suje su buɗe babban gate yanda sojojin zasu ji daɗin shugowa,. cikin gaggawa kuwa macije sunfi million duk sun hallaru a harabar masarautar bayan sun buɗe gate ɗin layi sukayi domin dasu za'a fara yin yaƙin kafin azo kan ogan nasun wato Munafurr, shi kam sarki Raamud bai ma san za'azo yaƙar shi ba... Rundunar motor Egwa ne na sojoji sun kai dubu ɗari suka tunkaro masarautar... (Egwa pah masu bindigu a saman mota, mota mai kakin soja wanda bindigarsu yake bada harsashin wuta😳😳).. A bayan motocin Egwa kuma still motar sojojin ne suma sun tafo a jere zasu kai su ɗari biyu iya motoci kawai suma masu jikin kakin soja suna tattare da boma-bome masu tarin yawa, Angel da Adity da Rumana su duk ɗin su suna daga cikin motocin indai macen soja ce toh tana cikin mota... A bayan motocin kuma sai waɗanda suka hau Dokuna🐎🐎🐎🐎🐎! wasu Dokuna ne masu ƙirar ƙarfi, ɓaƙaƙe dasu suma zasu kai su dubu ɗari, waɗanda suka hau Doki an ware ƙarfafan sojoji ne jarumai aciki kuwa har da Ogah Junaid, shima yana daga saman Doki.... A bayan Dokuna kuma taron sojojine waɗanda suke tafe da ƙafafuwansu, sai gudu suke ci da bindigoginsu a hannu.... Saman su kuma elekwabta🚁🚁🚁🚁 ne mai kakin soja zasu kai guda hamsin suma sojoji ne aciki (Ikon Allah duk wannan gayyar a mutum ɗayane🤔🤔) Shima Munafurr ya haɗa gayyarsa wato wani irin shiri yayi musu, Manya-manyan Jegaru ya nemo masu aman wuta da fikafikunsu sun kai su ɗari biyu a jere a wajen masarautar, Bayan jegarun nan kuma sai mikiyoyi masu carkwane idanun mutane suma sun kai su ɗari biyu ajere.. Bayan su kuma sai kadoji (corocodise) irin masu cinye mutane suma a jere suke sunkai su ɗari biyu.. Bayan su kuma sai Diragogi🦖🦖🦖🦖 suma sun kai ɗari a jere.. Bayan su kuma sai macije masu dafin bala'i, sara ɗaya suke yiwa mutum ya rasa rayuwarsa, suma suna nan a jere sun kai million.... daga su kuma sai a fafata da Munafurrr... ***** Mommy daga Nigeria Alwala tayo sannan ta tsai da sallolin lafula tareda jero addu'o'i, tana faɗin "Allah ya tsare sojojin da suka fita yaƙin nan, Allah ya dawo dasu lafiya, Allah ya basu nasara..." Itama Ayush zuwa tayi tayo alwala itama ta fara sallolinta na neman kariya daga wajen Ubangiji... tana addu'a Allah ya tsare mata iyayenta domin tasan yanzu mahaifinta bashida wani ƙarfin iko... Munafurr Allah Allah yake sojojin nan su iso a fara fafatawa, domin ya tanadar musu da abubuwan mugunta, kamar yanda suma sojojin suka haɗa runduna guda... Har yanzu kuma Damusa yana nan a ɓoye guri ɗaya ga kuma takobi a gabansa.... *Amm nace baa Ina masu fita yaƙi acikin readers nace how market🙌🙌* *Masoyan Junaiduu ban hango ku ba👀 shin kunata inaa?* *Cikin Egwa ne ko kuma kuna cikin motoci kodai kuma kuna kan Doki ko kuma kuna daga sama cikin elekwabta kodai kune a ƙasa masu gudu da ƙafafuwan ku?...* *Masu cikin elekwabta kune gawar farko domin jegaru masu aman wuta furawa suke yi🤣🤣* *Ga kuma mikiyoyi masu cire eyes😳😳😳* Toh masu karatu anan zan dakata sannan na tafi hutun sati guda, na barku lafiya... 𝑡𝑦𝑝𝑖𝑛𝑔✍️ 𝗠𝗔𝗧𝗔𝗥 𝗗𝗔𝗠𝗨𝗦𝗔 the wife of a tiger🐅🐅🐅🐅 𝙼𝚊𝚕𝚕𝚊𝚔𝚒𝚗 𝙰𝚜𝚖𝚎𝚎𝚝𝚊𝚑 ✍️✍️ 𝙿𝚊𝚒𝚍 𝚋𝚘𝚘𝚔 𝚌𝚊𝚕𝚕 𝚘𝚛 𝚠𝚑𝚊𝚝𝚜𝙰𝚙𝚙 09065443871 *💫💫{{N W A}}💫💫* Book two C̶h̶a̶p̶t̶e̶r̶ 31 ➡️ 32 Munafurr ganin sojojin sun kusan isowa yasa Dabbobinsa suka fara kai musu farmaki, Dragon's 🐉🐉🐉🐉 ne suka fara tashi sama sunkai ɗari biyu suka nufi wajen rundunan sojojin, Sojoji kuwa suna ganin abubuwa sun nufosu anan suka fara fitar da bindigoginsu suna harbawa, suma Dragogin haka suke amayar musu da wuta, ga kuma jegaru suma suna bata nasu wutan, suma sojojin wasu suna harbi wasu kuma suna guduwa, haka motocin sojojin nan suka fara tashi sama suna bom kasancewar akwai bomabomai acikin motocin, tin daga nan aka fara asarar rayukan sojoji saboda motocin da suke ƙonewan akwai sojoji aciki, waɗanda suke sauran motocin da wuta bai taɓa su ba haka suka rinƙa fitowa daga cikin motocin suna harbi kamar ruwan sama, suma jegarun an harharbesu domin dragon's da jegaru an harbi sun kai ɗari saboda yawan harbin da ake musu, Acikin motor gudà kuwa wata soja ɗaya ce take ciki bata fito ba sakamakon ƙafarta daya maƙale a tsakanin ƙarfe da ƙarfe na cikin motar, sai ihu take tayi ganin ko wani mota ƙonewa yake, tana ta ƙoƙarin cire ƙafarta amma ta kasa, sauran sojojin kuwa kowa ƙoƙarin ceton ransa yake ko sauraronta ba'ayi ba, tana cikin wannan halin sai ga Junaid ya nufo gurinta akan doki da gudun gaske zai cetota, kafin ya isa gurin kuwa har wani jegarin ya huro wutan bakinsa kan motar wuta da bom sun haɗu lokaci guda motar ta tashi sama tana kamawa da wuta ga sojar nan tana ciki sai faman kurma ihu take, A razane Junaid ya ƙwalla ƙiran sunanta da ƙarfin gaske ya furta "Rumaaanaaaa...." daiden lokacin motar ta faɗo ƙasi ta dagargaje! hatta shima Junaid saida ya yi sama shida dokinsa suka doku a ƙasi tsabar ƙarfin boom ɗin daya tashi da motar, cikin firgici ya ɗago yana ƙiran sunanta "Rumana! Rumanaa!! Rumanaaa!!!...". Rumana kuwa tintinin ta dagargaje ita da motar babu sauranta, motar kuwa sai ci da wuta yake... wani Dragon ne yazo ta bayan Junaid ya buɗe bakinsa ya amayo masa da wuta lokaci guda Junaid yayi wani irin juyi ya saita bindigarsa ya fasa masa kai da harsashi, takaicin mutuwar Rumana ne yasa ya harzuƙo ya fara harbin jegarun nan kamar mai, gani kake sunata faɗowa daga sama zuwa ƙasa, jegaru sunkai hamsin suka rufo kan Junaid suna hura masa wuta, wani irin juyi Junaid yakeyi yana tashi sama tareda faffasa musu kai, waɗanda suke cikin jirgi kuma tinin an rufe babinsu duk an ƙoƙƙone musu jirgaye da mutanen dake ciki duk da suma sunyi iya ƙoƙarinsu sun kashe jegaru da yawan gaske, rabin sojoji duk sun mutu daga yaƙin farko, wasu kumá duk sun koma dá báyá sun gudu kuma yawancin su sojoji mata ne waɗanda suka gudu aciki kuwa har da Adity itama ta gudu, iya waɗanda suke yaƙin ƙalilan ne basuda yawa daga Junaid ne sai Angel itama tana ƙoƙari sosai domin ta kashe dragon's ba adadi.. da haka duk saida suka gama da jegaru da dragon's ya rage babu ko ɗaya, Angel juyowa tayi ganin mutanensu da yawa a kwance babu rai yasa Angel tsorita sannan ta dubi kansu iya waɗanda suke nan bazasu wuce su hamsin ba, kuka Angel ta fara yi tana faɗin "dan Allah kuzo mu juya, kunga bamuda yawan sojojin, kuma bamu san mai zamu tarar a gaba ba..." Gaba ɗayansu ja da baya suka soma yi sun ɗauki maganar Angel, Junaid ya dakatar dasu da cewar "lusarai ne idan sunje gurin yaƙi suke guduwa, sojoji babu tsoro a zukatansu saboda haka ku saki jikinku insha Allahu mune da nasara, kamar yanda aka umarce mu damu kawo sarki Raamud haka kuwa zamu kamo shi dumu dumi a hañnu, idan kuwa bai kamu ba sai mu dagargaza masa kai shikenam..." Daganan suka saki jikinsu, a mata kuwa Angel ce kawai take nan amma sauran wasu sun mutu wasu kuma sun gudu.. Junaid ne ya kalli Angel sannan yace "ina camera?.." irin mai hango abu daga nesa,. tace "gashi nan ta miƙa masa.." Saitawa yayi a idonsa ɗaya yana hango irin abubuwan da aka tanadar dasu, Junaid jinjina kansa yayi yace "kowa ya zauna akan shirinsa, kowa ya saka hular glass saboda akwai manya-manyan tsuntsaye masu cakan ido, sannan a tanadi boms domin akwai corocodiles da kuma macizai...." wani ne a ciki yace "Oga ina dai ba Aljanu? inhar babu toh abun zai zo da sauƙi...." Junaid yace "wasu su shiga Egwa da zaran mun isa saiku fara harbi ku tattaka su da motar, wasu kuma su hau doki tinda akwai sauran dokunan..." haka kuwa akayi ita Angel motar ta shiga ta miƙe tsaye tayi ready da bindigarta... Su Junaid sune tafiyar farko domin sune akan dokin, basu fi su ashirin ba masu dokunan, waɗanda suke cikin motár Egwa kuma an barsu a baya saboda rashin gudun motar amma daga nesa zasu rinƙa harbi har su iso gurin, Mikiyoyi kuwa haka suka rinƙa tashi sama suna kai musu yakushi da carkwala, sojojin nan haka suka rinƙa harbesu suna faɗowa ƙasi, shi Junaid bai tsaya harbi ba kai tsaye wucewa yayi da gudu yana rataye da bindigarsa ga kuma jakar bom yana riƙe dasu, so yake ya tsallake gate ɗin domin a rufe yake, shi kuma wanda za'a yaƙa yana ciki, toh shi da Ogan yake so ya yi bada dabbobi ba, dayazo gurin corocodiles haka ya rinƙa jefa musu bom yana samun hanyar da zai wuce, duk suna kawo masa hari sosai yana kauce musu da haka ya tsallake su, yazo kan macijai suma bom ya rinƙa jefa musu, yana gudu da dokinsa, macizai kuma tsabar na masifa ne haka suke tashi sama suna sarar dokinsa, shi basu samu isoshi ba saboda miƙewa tsaye yayi akan dokin yanda maciji bazai taɓashi ba domin sara ɗaya suke wa mutum, Junaid daƙer dokinsa ya ƙarasa dashi waran ginin masarautar a yayin da dokin yake shirin faɗuwa tsabar saran da macijai sukayi mishi, a lokacin kuma Junaid yayi wani irin tashi sama kamar mai furawa haka ya yi sama sosai ya kamo wani ƙarfen jikin ginin masarautar wanda yake rabin tsayin ginin, ba ƙaramin dogon gini akayi wa masarautar nan ba, duk tashi saman da Junaid yayi amma a iya rabin ginin ya tsaya, haka ya rinƙa jawuwa yana ƙara yin sama, yanason tsallake ginin... Sojojin da suke ƙasi kuwa wasu sake baki sukayi suna kallon Junaid, suna kuma mamakin yanda suka ganshi yayi tsalle ya tashi sama kamar ɗan China ko kuma super man ko bad man ko spider man, suna cikin wannan tunanin kusan su goma haka kadoji suka rinƙa kayar dasu suna fata-fata da naman su, yayin da wasu kuma suke fafatawa da mayaƙan dabbobin, Angel ce ta ƙwalla ƙiran Junaid tana faɗin "wannan wani irin garaje ne, ina zaka iya tsallaka katangar nan? zaka iya faɗowa fa kuma idan har ka faɗo sai dai ƙashshushuwanka...." ta ƙarasa maganar itama tana mamakin yanda yahau wannan katangar mai uban tsayi ga tsantsi duk jikinsa..." wani kada ne yayo kanta tareda buɗe bakinsa zai rufa mata a fusace Angel ta wurga masa bom a cikin bakinsa nan danan corocodile ya dagargaje haka ta cigaba da faffasa musu kai da harsashi, wasu kuma suna jejjefa musu bomabomai, Junaid gaba ɗaya ya gaji sauran masa kaɗan ya isa saman katangar, yana riƙe da ƙarfe wanda yake riƙe da katangar, yana sauƙe numfashi ya sunkuyar da kansa ƙasi yana kallon abunda ke faruwa ata ƙasa, zaro ido yayi waje cikin firgici ya furta "innalillahi wa inna ilaihi raju'un, oh my God..." Ganin duk anyi fata-fata da sojojinsu iya mutum uku ne kawai suka saura, daga Angel ne sai maza biyu sune suketa faman faɗa, dan ma dabbobin duk suma sun ƙare corocodile ɗaya ne ya saura sai macijai dake sunfi sauran yawa amma suma an ƙarar da fin rabin su, sojoji maza biyun ne suketa aikin jefa musu bom a macijen nan, ita kuma Angel crocodile wanda ya rage ne yayo kanta da zafinsa, ga babu bom a hannunta sannan bindigarta ya faɗi babu halin ɗauka yana tsakiyar macijai, Junaid kallonta yake domin shikam har ya fidda rai akan rayuwarta, Crocodile ɗin ne yayi sama tukun ya faɗo mata a kanta ya danneta bakinsa a saitin wuyanta zai datsa mata wuya da haƙwaransa masu kaifin bala'i, Haka zuciyar Junaid yake bugawa da ƙarfin gaske, jikinsa na rawa kamar zai faɗo ƙasa,. zuba wa crocodile ido yayi wanda ya rufe Angel gaba ɗaya ba'a hangota, ganin corocodile baya motsi abun ya ɗaure masa kai, sai can bayan wasu mintuna idon Junaid still yana kansu yaga crocodile yana motsi lokaci guda kuma saiyaga an ture shi gefe ga jini yanda yaketa tsiyaya daga wuyansa, Angel ce ta tureshi gefe ta tashi zaune tana jan numfashi ga duk jinin crocodile ya ɓata mata jiki, Junaid daga nesa yake kallonta cikin mamaki yace "how comes?..." ba tareda ta jiyoshi ba domin yayi nisa da ginin sosai.. Tunani ya shiga yi yanda abun ya kasance wato a lokacin da crocodile ya rufo kanta ta rigada ta cire wuƙar jikin takalminta ta cakawa crocodile a wuya, bataji ciwo ba sai kurzuwan da tayi... Junaid murmushi yayi ya furta "gud jaruma ta..." da ƙarfin gwiwarsa ya cigaba da yin sama, suma sauran sojojin da suka rage su biyun murna sukayi ganin Angel bata mutu ba, domin tana temaka musu sosai, babu wanda zai iya yin faɗan da tayi... Angel hango bindigarta tayi a cikin macijen kamar wanda ake ƙara yawansu, ɗaya daga cikinsu ne ya kalli Angel a tsorace yace "Madam bom fa ya kusan ƙarewa sauran guda goma kuma naga macizen da sauransu, Angel ta miƙe tsaye tareda faɗin "zanyi maganinsu kuwa yanzu zasu ƙare..." ta karɓi sauran bom ɗin tace dasu "ku fara aiki da bindiga, Ni kuma zanji dasu da wannan bom..." duk faɗan nan da takeyi da jaka a bayanta ta sauƙe jakar ta ciro takalmin mai taya, sannan ta cire takalmin ƙafarta ta sanya maitayar ta miƙe tsaye da jakar bom a hannunta ta rufu kan macijen nan da gudun gaske tana mummurƙuse su da takalmin tayanta tareda jejjefa musu bom, da zaran maciji ya kawo mata sara saita zamar da ƙafarta tana wasan gudun takalmin taya akansu... maza biyun nan haka suka tsaya suna kallonta ga yanda take bada action Kamar a film, shima Junaid kallon ƙasa yayi yaga irin abunda Angel takeyi smile kawai yayi a daiden lokacin har ya isa sama ya zauna yana hutawa, cikin ƙanƙanin lokaci Angel ta gama da macijen nan tas sai gawarwakinsu dake wajen kaca-kaca, tana gamawa tazo ta cire takalmin tayan ta mayar cikin jakarta sannan ta maida asalin takalminta na soja, suna tsaye suna jiran Junaid ya haura ya buɗe musu gate su fantama cikin masarautar domin ta ciki aka kulle, Junaid igiya ya ciro shima daga cikin jakarsa ya ɗaure a jikin ƙarfen saman gini sannan ya kama igiyar nan ya fara sulalowa ƙasi ta cikin masarautar haka har yaje ƙarshe, yaji babu alamun motsin mutum ko ɗaya, hannu yasa ya buɗe gate ɗin da ƙarfin gaske yake tura gate ɗin zai buɗe, suma su Angel ɗin tafowa sukayi da gudu suka sa hannu kowa yasa ƙarfinsa aka buɗe gate ɗin gaba ɗaya, Bayan sun shige cikin masarautar tsayawa sukayi suna tunanin ta yadda zasu fara kutsawa ciki, Junaid yace "kowa ya riƙe makaminsa da gaske saboda wannan yanada hatsari sosai..." Ɗaya daga ciki yace "dan Allah kasa a turo mana wasu sojojin, mu kaɗai bazamu iya da wannan ba, mu huɗu ne fa kawai muka rage..." Junaid yace "taya za'a turo su bayan babu waya a hannun mu duk sun faɗi..." ******** Sarki Raamud kuwa shida matarsa duk sun ruɗe jin tashin bomabomai da ƙarar bindiga, Uma Bara'at kam sumar ta sau uku jin halinda ake ciki ga tsohon ciki, tana kuka tareda faɗin "shikenam mun mutu an kawo mana farmaki, nasan bazamu bar nan a raye ba..." Sarki Raamud yana rarrashinta yace "ki kwantar da hankalinki tabbas ni sukazo farmaka amma kuma akwai wanda zai tari faɗan, yanzu haka nasan yaƙin ya koma kan Munafurr..." Daƙer ya rarrasheta tayi shuru, suna cikin wannan halin suka ji an buɗe ƙofa, ganin Munafurr ne yasa duk suka razana, kafin suce komai Munafurr ya riƙo wuyan sarki Raamud ya ɗagashi sama da hannu ɗaya sannan ya cabko wuyan Bara'at itama ya ɗagata sama tana lilo da sawayenta ga ciki ɗurumma a gaba ya girma sosai! Haka yayi waje dasu a haka yana riƙe dasu da hannu ɗaɗɗaya, ita kuwa Bara'at har numfashinta ya soma ɗagewa, ya fito a fusace domin ransa ba ƙaramin ɓaci yayi ba ganin duk an tarwatsa masa mayaƙan dabbobinsa, yana fitowa harabar masarautar yanda su Junaid suke a tsatstsaye, ganin Munafurr yasa duk suka razana, haka ya wurga sarki Raamud da Bara'at gaban su Junaid, Bara'at ihu takeyi saboda cikinta ba ƙaramin buguwa yayi ba tana faɗin "wayyo cikinahhh, innalillahi wa inna ilaihi raju'un cikina zan mutu..." Junaid kallon Bara'at yake yana tuna mahaifinsa da tayi sanadiyar mutuwarsa, sannan ya juyo yana kallon sarki Raamud wanda shine silar rashin lafiyarsa kuma shine wanda yake wahalar dashi, tsananin tsanarsu ne ya ƙara shiga masa zuciya, Idonsa ya ɗaga yana kallon Munafurr ji yayi Angel ta ƙanƙame shi tana faɗin "wallahi Oga Junaid ba'a turomu mu yaƙi wannan basamuden dodon ba, mu rufawa kan mu asiri mu kama waɗanda ake nema...." Junaid duk yana jin abunda Angel take faɗa amma bai bata amsa ba, Sauran sojojin guda biyu kuma duk fitsari suka sau a jikinsu ganin halittar Munafurr a yayin da kuma ɗaya acikinsu ya makance tsabar irin kallon da yake yiwa Munafurr, sai ihunsa akaji yana murtsika idonsa tareda faɗin "wayyo ido na, wayyo idona bana gani wallahi, duhu nake gani..." yanata lalumen mutane, lokaci guda kuma yayi tsitt ya ƙafe a guri ɗaya sakamakon ƙarfen da Munafurrr ya wurgo masa ya soki maƙogaronsa ya faɗi ƙasi matacce, Junaid zaro ido yayi waje yana kallon ɗaya daga cikin sojojinsa wanda aka masa wannan ɗanyen hukunci... Ita kuwa Angel ƙara ƙanƙame Junaid tayi jikinta na kakkarwa tace "idan kuka haɗa ido dashi zaku makance, Munafurr ne mungun mutum ne wannan anban labarinsa....." Munafurr wani ƙarfen kuma du ya wullowa Angel jin tana magana sauran kaɗan ƙarfen ya shige mata goshi Junaid yayi saurin cabkewa sannan ya wurgar gefe, duk wanda yayi magana haka yake wannan hukuncin, Bara'at kuwa tintinin sarki Raamud ya toshe mata baki.... Munafurr da ƙwayar idonsa ya rufe babban gate ya kulle yana wani irin dariya yana cewa "yau kun shugo masarautar sarki munafurr, nine mai wannan masarautar kuma anan zan bisine gawarwakinku...", yana mai ƙara tintsirewa da dariya, ɗayan soja ne ya ɗago bindigarsa ya fara harbin Munafurr kafin bullet's su ƙarasa gurin Munafurr har ya juyar da bullet da ƙwayan idonsa sun koma kan sojan da yayi harbin, lokaci guda shima ya faɗi matacce, Yanzu iya Junaid da Angel ne suka rage sojoji! Ga Uma Bara'at kwance kan cinyar Sarki Raamud sai murƙususu take tayi cikinta ba ƙaramin ciwo yake mata ba, tana jin yanda twins ɗinta suke mata juyi a ciki...... *WAƊANDA AKAYI YAƘI DASU NACE BAAAA HOW MARKET🙌🙌* *Naga iya Angel da Junaid ne suka tsira a yaƙin waje kodai kuma an sheshsheƙeku ne ko kuma kun bi Adity kun gudu🤔🤔* Wai shin kunga laifin Aditi data gudu kuwa? Nidai banga laifinta ba yaciin🤣🤣🤣 Akwai waɗanda basa comments dalilin da yasa nake hutawa kenam wallahi, Mutane kusan 50 amma bazaka samu mutum 10 waɗanda zasuyi maka sharhi ba haba dan Allah.. Duk temakon kai ne dai, zaku karanta abu amma ba liking bare comment Kodan gadararku kun biya kuɗi ne🤔🤔 Amma ai nima idan akayi mun godiya zanji daɗin yin typing next Dan Allah ku gyara wannan bayi bane, mu kyautatawa junan mu shine zaman tare.... 🙏🙏🙏🙏🙏🙏 𝑡𝑦𝑝𝑖𝑛𝑔✍️ 𝗠𝗔𝗧𝗔𝗥 𝗗𝗔𝗠𝗨𝗦𝗔 the wife of a tiger🐅🐅🐅🐅 𝙼𝚊𝚕𝚕𝚊𝚔𝚒𝚗 𝙰𝚜𝚖𝚎𝚎𝚝𝚊𝚑 ✍️✍️ 𝙿𝚊𝚒𝚍 𝚋𝚘𝚘𝚔 𝚌𝚊𝚕𝚕 𝚘𝚛 𝚠𝚑𝚊𝚝𝚜𝙰𝚙𝚙 09065443871 *💫💫{{N W A}}💫💫* Book two C̶h̶a̶p̶t̶e̶r̶ 33 ➡️ 34 Angel tana ƙanƙame da Junaid tana ta Addu'a idonta a rufe, Junaid ya kawo kansa saitin kunnenta yace "ki zamo jaruma, kisa a ranki zaki iya yaƙar wannan ma..." bai ƙarisa maganar ba yaji Munafurr yana cewa "Junaiduu idan kana son fita daga cikin masarautar nan da ranka toh sai kayi mun abu ɗaya! da hannunka nake so ka kashe sarki Raamud a yanzu babu jira..." Junaid abun mamaki ya bashi, kallon sarki Raamud yayi yana mai jin takaicinsa sannan ya kalli Munafurr yace "inda ace anban damar na kashe shi ai da yanzu babu labarinsa saboda kallonsa ma banaso nayi, yanzu a raye ake buƙatarsa..." Munafurr yace "kaii yaro kar kamun tirjiya kayi abunda na saka ka.." "Shaiɗani baya bani umarni nabi..." a cewar Junaid. tintsirewa da dariya Munafurr yayi yana faɗin "idan baka kasheshi ba ni zan kashe ka..." ya ƙarasa maganar yana cillo wa Junaid takobinsa, cikin nuna jarumta Junaid ya kaicewa takobin tareda yowa kan Munafurr da gudu zai naushe shi daman yana jin takaicin kashe masa sojoji da yayi a gabansa, yana zuwa kuwa Munafurr yasa hannu ya cabke wuyan Junaid ya ɗaga shi sama da hannu ɗaya, Junaid ƙoƙarin ƙwace wa yake yi amma ba hali domin ba ƙaramin riƙo akayi masa ba, Angel saita Munafurr tayi da bindigarta ta harba, Lokaci guda Munafurr ya cabke bullet da ɗayan hannunsa yana karya wuya idonsa akan Angel ya ƙara tintsirewa da dariya yana faɗin "kee zaki iya dani ko?.." Angel fashewa tayi da kuka ta durƙusa da gwiwowinta, shi kuwa Junaid ƙafarsa ne yake ta lilo ya gagara ƙwacewa daga shaƙar da Munafurrr yayi masa ana cikin wannan halin har Junaid ya fara fita hayyacinsa lokaci guda Munafurr ya cillashi gefe sakamakon mashin da aka caka masa ta bayansa, kafin ya waiwaya an ƙara caka masa! Munafurr waiwayawa yayi yana kallon sarki Raamud wanda ya zagaya ba tareda kowa ya saniba yaje ya ɗauko takobi da mashi ya wurga wa Junaid da Angel yana faɗin "ku tashi ku yaƙi wannan shaiɗanin mutumi marar tausayi idan baku kashe shi ba to shi zai kashe ku..." shima yana riƙe da nasa takobin zai ƙara caka masa yaji Munafurr yayi wurgi dashi gefe guda yasa hannu yana cire mashin da sarki Raamud ya caka masa a fusace ya miƙa hannunsa saiga takobinsa shima ya tafo gareshi ya cabke shi, Junaid miƙe wa yayi yana maida numfashi hannunsa riƙe da takobin da sarki Raamud ya wurga masa, itama Angel miƙewa tayi saiga sarki Raamud shima ya taso duk suka jeru suna fuskantar Munafurr, Uma Bara'at kam tana gefe guda tana zaune sai kallon Junaid take wanda goshinsa yake ɗaure da jan ƙyalle, ta gane ƙyallen Ayush ce itama Ayush daga wajen umanta ƙyallen ya fito wato ita kanta Bara'at, sai dai ba haka kawai Ayush ta ɗaurawa Junaid ƙyallen ba akwai saƙo a tattare da wannan ƙyallen... Junaid da sarki Raamud ne suka rufa gurin Munafurr da gudu suka fara kai masa sara shima haka yake binsu da takobinsa har ya sari Junaid a ciki yayin da ita ma Angel ta rufa masa ta sari ƙafarsa saboda Munafurr ba ƙaramin tsayi ne dashi ba duk ɗinsu a kunkuminsa suka tsaya, Munafurr jin zafin sarar da Angel tayi mishi ne yasa yakai mata canki itama tayi baya tana birgima, shima sarki Raamud saida ya saita wajen penus ɗin Munafurr ya caka masa wuƙar, wani irin ihuu Munafurr yayi har saida duwatsu suka fara girgiza a fusace Munafurr yakai sara wa sarki Raamud badan sarki ya kaice ba babu abunda zai hana Munafurr ya fille masa kai, Junaid ne shima ya tashi ga jini yanda yake zuba masa domin ba ƙaramin yankuwa yayi a ciki ba Allah yaso ba caka wa akayi ba, ya ƙwalla ƙiran Angel yana faɗin "ki miƙe mu gama da wannan matsiyacin.." wani irin tsalle Angel tayi ta miƙe tsaye da takobinta a hannu ta tafo gurin Junaid da gudu yayin da shi kuma ya sauƙe tafin hannunsa ɗaya ƙasi tana zuwa ta taka hannunsa ya ɗagata sama ya cillata wajen Munafurr ta ƙara yin sama tayi wani ihu ta dage ta sari hannunsa daga saman kafaɗa nan take saiga hannun Munafurr ɗaya ya faɗo ƙasi, kafin Angel ta sauƙo ƙasa kuwa Munafurr ya juyo a wahale ya kai mata sara a wuyanta da hannunsa ɗaya mai riƙe da takobi sannan ya canketa gefe saida tayi sama kamar ƙwallo zata faɗo ƙasi Junaid a ruɗe yayi wani irin ihu yana ƙiran sunanta "Anngeeelll...." ya yo kanta da gudun gaske kafin ta ƙarasa faɗowa ƙasa yakai hannu ya cabketa sukayi ƙasi a tare yana rungume da ita ga jini kuwa yanda yaketa tsiyayowa daga wuyanta ga shatar yankan da akayi mata a wuya ya yanke mata maƙogaro dan ma bakin takobin ne ya sareta da wuyanta zai sare mata gaba ɗaya, Jikin Angel ne yake kakkarwa sosai murya na rawa daƙer take faɗin "mutuwa zanyi! mutuwa zanyi!! mutuwa zanyi!!! innalillahi wa inna ilaihi raju'un, Ogah Junaid ka te te temake niiii...." Shima Junaid hawaye yake yi yana faɗin "bazaki mutu ba Angel insha Allahu zaki tashi kinji..". Angel dishi-dishi ta fara gani idanuwanta suna shirin rufewa bakinta na kakkarwa a hankali take furta "Laa i la ha illa llaa mu ha mma du raaasulullaahh.....". ta cacumi Junaid sosai daga nan bata ƙara motsi ba ga baki a buɗe kamar wacce zatayi magana abunda ta gama furtawa last kenam rai yayi halinsa, ga ido a buɗe tana kallon sama!!!! A hankali Junaid ya furta "Angel.." bakinsa na kakkarwa jikinsa ne gaba ɗaya yahau ɓari yana jijjigan Angel tareda faɗin "No! no!! noo!!! noooo!!!! kar ki tafi Maryam Please help me don't leave me aloneeee...." wani irin ihuu Junaid yayi, kuka yake sosai kamar wanda ransa zai fita yana rungume da Angel sosai a jikinsa, Rumana ce ta fara masa gizo ga kuma Angel idonsa a ƙanƙame, haƙwarensa ne suka fara kakkarwa suna dukan juna tsabar raɗaɗin da yake ji acikin zuciyarsa.... Sarki Raamud ne yake ta fafatawa da Munafurrr shima sararsa akayi a saitin ƙirjinsa sannan aka wurga shi gefe, tintsirewa da wani irin mahaukacin dariya Munafurr yayi da hannunsa ɗaya, idonsa akan Junaid wanda yake rungume da Angel, Munafurr da takobinsa ya saita Junaid sannan ya wurga masa takobin kafin takobin ya iso ya soki Junaid Bara'at ta tafo da gudun gaske ta rufa kan Junaid tana juyowa kuwa wannan takobin ya shige cikinta, wani irin ƙara Bara'at tayi ta yo báyá ta kwanta a jikin Junaid ta bayansa yaji sauƙar mutum a kwance, juyowa yayi a tsorace yana gudun abunda zai gani domin ihunta ya girgiza masa kunne, ido ya zaro waje baki a buɗe ganin Mata ga tsohon ciki ta sadaukar da rayuwarta akansa, wuƙar gaba ɗaya ya lume a cikinta sai ƙotar wuƙar a waje!! Da gudu sarki Raamud ya tafo gurin yana ambaton sunata ya ɗagota daga kan Junaid ya kwantar da ita a saman cinyarta ya rungumeta sosai da hannu ɗaya, ɗayan hannun kuma yana rungume da tsinin cikinta ya kasa furta komai sai ido da yaketa zarowa, hankalinsa ne ya fara barin jikinsa, ƙwaƙwalwarsa ce take juyawa, sarki Raamud gaba ɗaya ya fita hayyacinsa ko kuka ya kasa yi... Junaid ne ya ƙwantar da Angel ya tashi yazo gaban Bara'at ya durƙusa sannan yasa hannu ya zaro takobin da yake nitse a cikin ta, lokaci guda shima ya ƙara fashewa da matsanancin kuka ga jan ƙyalle a ɗaure da goshinsa, Wani irin ihuuuu Munafurr yayi na azaba Junaid yana durƙushe ya fara ji suna girgiza, tsabar ƙarfin ihun Munafurr a gigice Junaid ya waiwaya yana kallon gurin da Munafurrr yake a tsaye yaga wani halittar Mutum ne ya caka masa takobi na tsafi ta bayansa, ga yanda takobin yake fidda farfatsin haske, zaro takobin yayi sannan ya ƙara datsa masa a saitin zuciyarsa still wannan takobin yana bada haske, wannan mutumin ba kowa bane face *NARASIMHA* ga kuma Damusa shima yana tsaye ta gefen Narasimha,. Junaid sake baki yayi yana kallon Narasimha cike da mamaki yana maganar zuci "wannan wani irin halitta ne shima? mutum mai kama da biri..." Narasimha yana zare takobin Munafurr ya faɗi ƙasi ya durƙusa da gwiwowinsa,. Narasimha ya kalli Junaid yace "ka tashi kazo ka cire masa kayi da hannayenka yaa Sarkin wannan masarautar na gobe...". Junaid ɗaukar takobi yayi ya riƙe sosai tareda tahowa da gudun gaske a fusace ya taka kafaɗar Munafurr yayi tsalle ya fille masa kai sannan ya dirƙo ƙasi yana huci, Kayin Munafurr ne ya faɗo ƙasi, gangan jikinsa shima ya faɗi, Junaid zuwa yayi wajen da kayinsa yake a yashe ya saita idanuwan Munafurr masu hatsari ya caccaka musu wuƙa, shikenam an gama da rayuwar Munafurr! Narasimha yana kallon Junaid yace "ba dan wannan Damusan ba da bazaku samu tsira ba gaba ɗayanku, domin shi yake ajiye da wannan takobin mai tasirin gaske a gurinsa, wannan mutumin bazai taɓa mutuwa ba indai ba'a yi aiki da wannan takobin ba, na zo ni ne domin na kawo muku agaji yanzu kuwa zan tafi, zan koma daga yanda na fito saboda ba'a duniya nake zaune ba, kwanana ya daɗe da ƙarewa daga zaman nan duniya sakamakon rashin wannan takobin..." ya ƙarasa maganar yana nuna takobin hannunsa, ya fiddo da wani ƙaton littafi ya miƙawa Junaid yace "ga wannan karɓi.." Junaid ya karɓa sannan Narasimha ya cigaba da cewa "kaine magajin wannan masarautar, duk abunda kake son sani akan wannan masarautar toh wannan littafin ya ƙunshi komai a ciki, idan kanason yin tambaya to duk amsoshinka yana cikin wannan littafin, nasan baka san asalin mahaifinka ba to ka duba wannan littafin domin shine ɗan asalin mai asali, kakanka wanda ya haifi mahaifinka shine sarkin wannan masarautar shine wanda ya mulki mutanen wannan ƙasar, wancan mutumin wato sarki Raamud wanda kake ƙiyayya dashi shine ɗan uwan mahaifinka domin sun kasance ƴan biyun kakanka ne, yana da ƴa mace guda ɗaya wanda suka haifa shi da matarsa Sarauniya Bara'at wacce Allah ya karɓi rayuwarta a halin yanzu, Gimbiya Mayushaert wacce kake tareda ita a gida itace ɗiyarsu, wannan littafin ni na rubuta shi da hannuna daga farko har ƙarshen labarin zaka gani, da zarar ka kammala karanta tarihin labarin zan ɗauke littafi na domin ban gama rubutuna ba kuma bazan gama ba har ƙarshen rayuwarku, wannan littafin na biyu ne littafin na ɗaya yana gurinka cikin ɗakinka kaje ka duba zaka gani, ga kuma amanar Damusa ka riƙe shi a wajenka domin amanar kakanka ne, na Barka lafiya sarki na gobe...." Narasimha yana kaiwa nan yayi ɓacewarsa ɓatt. Har saida Junaid ya tsorita, gumi ne yake yanko masa zuciyarsa cike da tambayoyi da al'ajabi gaba ɗaya kansa ne ya kulle yana wani irin tunani tunani ya furta a hankali "kenam mahaifina ɗan masarautar wannan ƙasan ne? toh amma taya mutane zasu fahimci haka? kenam sarki Raamud ɗan uwan mahaifi nane shiyasa ya addabi rayuwata a baya kenam? to amma wacece ɗiyarsa Gimbiya Mayushart? shin aina take?...". zuciyarsa cike take da tambayoyi ga hannunsa riƙe da littafi, ɗago kansa yayi ya kalli damusar dake kallonsa shima sai kallon juna suke shi da damusa,. Damusan ne ya tafo gaban Junaid ya tsaya shima Junaid sunkuyawa yayi ya ɗora hannunsa akan Damusan yana shafa shi, tsananin ƙaunar Damusan ne ya shiga zuciyar Junaid, miƙewa Junaid yayi ya nufi cikin fadar masarautar, shi kuwa Damusan nufan gurin sarki Raamud yayi yaje ya kwanta a kusa dashi ya ɗora kansa akan ƙafarsa, duk abunda Narasimha ya sanarwa Junaid sarki Raamud yana ji saidai babu halin yin magana domin yana alhinin mutuwar sarauniyarsa... Junaid yana shiga cikin fadar idonsa suka sauƙa akan babban photon dake manne a saman bango, zaro ido waje Junaid yayi da ƙarfi ya furta "Yushert..." yana girgiza kai yace "a'a ba ita bace amma kuma kamar dai ita ɗin ce, wallahi Yushert ce! itace wallahi Yushert ce!! daman tana da haɗi da masarautar nan? kenam itace Gimbiya Mayushart?...." yana cikin wannan halin yaji ƙarar jirgaye, da gudu ya fice yayi waje yaga har sun buɗe get sun shugo, ganin sojojinsu ne suka zo yasa yayi ajiyar zuciya ya furta "Alhamdulillah" Jirgaye ne sun kai ashirin suka zo kwasan matattun sojoji waɗanda aka rasa rayukansu, yana tsaye yana ganin an ɗauki Angel nan danan hawaye suka fara gangaro masa, haka yana kallon yanda aka ɗaga Bara'at yana tunanin "maiyasa ta zaɓi ta mutu akan ni na mutu? meyasa? Bayan nazo da niyar ɗaukan fansata akanta shine ita kuma ta bada rayuwarta akaina? kuma ga tsohon ciki a jikinta innalillahi wa inna ilaihi raju'un Allah ya gafarta miki na gode da sadaukarwarki agareni sarauniya..." Haka yake wannan maganar zuci har aka zo kan sarki Raamud yana ganin yanda aka ɗaɗɗaure shi da igiyar kaca saboda suna ganin shine mai laifin kuma shi aka kawowa farmaki, girgiza kai Junaid yayi yana kallonsa amma ya kasa ai watar da komai shidai acikin ransa yasan bazai taɓa bari a cutar dashi ba tinda yanzu ya shiryu kuma bayan haka mahaifi ne a waransa tinda ɗan uwan mahaifinsa ne, Munafurr kuma a leda aka tuttusa ɗan banza suka yanke shawarin za'aje can bayan gari a ƙone shi.. Junaid yana tsaye yaji wani daga cikin sojojin yace "Captain Junaid sannu da ƙoƙari, naga kaji ciwo sosai muje cikin jirgi a duba maka raunin..." Junaid ba tareda ya furta komai ba yayi gaba abunsa, yana dab da fita daga cikin masarautar yaji sojoji sun fitar da bindigunsu sun saita Damusa zasu harbeshi, a gigice Junaid ya ɗaga musu hannu yace "ku dakata Please...." ****** Ɓangaren su Ayushert Ayush ce take ta zirga-zirga a cikin ɗakinta zuciyarta sai faman harbawa take ga hawaye shaɓe-shaɓe akan fuskarta,. tana cikin wannan zirga-zirgar sai ga mommy ta turo ƙofar ɗakinta da sallama a bakinta tana sanye da hijab ganin Ayush a wannan halin yasa ta faɗin "lafiya kuwa Ayush meyasa kike ta faman zarya a ɗakin ko abincin rana baki ci ba gashi yanzu anata ƙiraye-ƙirayen sallar Isha'i, Ayush tafo wa gurin mommy tayi tana kuka tace "mommy ki taɓa zuciyata kiji zata fashe, bugawa take da ƙarfi hankalina ya kasa kwanciya inaji a jikina wani ya mutu..." Mommy tace "ki kwantar da hankalinki Ayush Insha Allahu babu wanda zai mutu duk zasu dawo lafiya ƙlau..." Ayush tace "a'ah Mommy sanyi nake ji na rasa wani ɓangare na jikina, akwai abunda ya faru, ba haka kawai ba..." Wayar Mommy ce ta fara ringing a hannunta, ɗaga ƙiran tayi gabanta na faman tsinkewa tana gudun abunda za'a sanar mata, "kar kuma a sanar mun mutuwar yaro nah.." hannunta na kakkarwa tayi picking call tareda karawa a kunne tace "hello officer Sadik..." sanar mata yayi akan taje ta kunna tv domin ganin labarai akan yaƙin da aka gudanar, "Amma Sadik Junaid fah yana nan lafiya kuwa?..." ya bata amsar cewa yana nan cikin ƙoshin lafiya sai raunikan da baza'a rasa ba... daga nan hankalin mommy ya kwanta ta katse ƙiran tareda jan hannun Ayush tace "zo muje muga labarai..." Bayan sunje sun sauƙa falon zama sukayi mommy ta kunna tv abunda suka fara ganin ana magana akai shine akan sojojin da suka gudu za'a sallame su a aiki sai lokacin da aka nemesu, gasu yanda akaita nuno photunansu har da Adity. Mommy dariya tayi tana faɗin "yanzu Adity duk faɗanki har ki gudo a gun yaƙi." Ita kuwa Ayush ko motsawa batayi ba balle ta murmusa fuskar nan ba Annuri ita kaɗai tasan abunda take ji a zuciyarta, A labarai aka nuno waɗanda suka mutu a cikin sojojin aka nuno photon Rumana wacce boom ya tashi da ita, Mommy ta girgiza sosai dajin mutuwar Rumana har da hawayenta, daga baya aka nuno Angel har da photon gawarta, Ba mommy ba hatta Ayush saida ta miƙe tsaye, mommy cikin firgici da tashi hankalinta a tashe tace "ehhhhh Angel ta mutu innalillahi wa inna ilaihi raju'un Angelll..." Ayush kam fashewa tayi da kuka tana faɗin "Aunty Maryam innalillahi wa inna ilaihi raju'un Allah ya jiƙanki Aunty Maryam" cikin kuka Ayush take magana, can sukaji ance mutum ɗaya ne ya tsira a cikin sojojin! Ƙirjin mommy ne ya buga da ƙarfin gaske domin tana tunanin Junaid ma ya mutu tinda ance mutum ɗaya ne ya tsira, itama Ayush dakatawa tayi da kukan tanason ganin wayene ya tsira kar taji cewa Junaid ɗinta shima ya mutu, gani sukayi an nuno photon Ogah Junaid, sannan anyi masa video gashi ga Damusa a gefensa, Sunyi farin cikin ganin Junaid a raye, mommy tace "toh aina ya samu Damusa kuma?..." Ayush gabanta ne yaketa faɗuwa kar ace an kashe mata iyayenta, amma ta gane Damusan mahaifinta, Gani tayi an nuno videon mahaifinta an ɗaɗɗaureshi da kaca anata jansa, ana sanarwa cewa an kamo babban mai laifi wanda ya gagari mutane.... Ayush hawaye ne ya fara wanke mata fuska ganin mahaifinta a cikin wannan yanayin, Mommy miƙewa tayi tsaye tana zaro ido waje gani tayi sarki Raamud kamarsu ɗaya da mijinta wato mahaifin Junaid, kamar wanda aka tsaga kara hatta tsayin sumar kayinsu, shima mahaifin Junaid lokacin da yazo Nigeria haka sumar gashinsa yake daga baya ya aske, Mommy ƙafarta ne ya fara kakkarwa ga hajijiyan da yake shirin ɗaukarta a hankali ta zauna akan kujera tana dafe da goshinta, ga hawaye yanda yake ta gangaro mata.... Ayush gani tayi an nuna photon Umanta da tsohon ciki a jikinta wai an kasheta, A zabure ta tashi tsaye tana zazzarowa ido ta furta da ƙarfi cewa "Umaaa, wayyo Allah nah Umaaa na ta mutu sun kasheta, Junaid ya cuceni ya kashe mun mamanaaa...." Mommy ji tayi Ayush tana wasu maganganu marasa kan gado, Lokaci guda kuwa Ayush tayi wani irin razanannen ƙara ta kama kayinta ta faɗi saman kujera sumammiya..... *AMMM NACE BAA HOW MARKET👋👋👋👋👋👋👋* *Toh nidai na feceee🏃🏻‍♀️🏃‍♀️🏃‍♀️🏃‍♀️🏃‍♀️🏃‍♀️🏃‍♀️* 𝑡𝑦𝑝𝑖𝑛𝑔✍️ 𝗠𝗔𝗧𝗔𝗥 𝗗𝗔𝗠𝗨𝗦𝗔 the wife of a tiger🐅🐅🐅🐅 𝙼𝚊𝚕𝚕𝚊𝚔𝚒𝚗 𝙰𝚜𝚖𝚎𝚎𝚝𝚊𝚑 ✍️✍️ 𝙿𝚊𝚒𝚍 𝚋𝚘𝚘𝚔 𝚌𝚊𝚕𝚕 𝚘𝚛 𝚠𝚑𝚊𝚝𝚜𝙰𝚙𝚙 09065443871 *💫💫{{N W A}}💫💫* Book two C̶h̶a̶p̶t̶e̶r̶ 35 ➡️ 36 Bayan kwana biyu da gama yaƙi Junaid yana zaune a bakin gadonsa na hotel ɗin sojoji dake ƙasar California, ga kuma Damusa a gefe guda yana kwance bayan ya kammala cinye kayan maƙulashe da aka kawo masa domin shi wannan Damusan baya cin ɗanyen nama, Junaid yana riƙe da littafin da Narasimha ya bashi a halin yanzu bazai iya karantawa ba har saiya koma gida tukun, burinsa shine ya koma gida yaga Mommynsa... Ga tunanin Ayush ya cike masa ƙwaƙwalwa gaba ɗaya ya kasa fahimtar ya lamarin yake, maganar zuci ya shiga yi yana faɗin "daman Yushert ɗiyar maƙiyina ne? daman mahaifinta ne ya turota akan tazo ta gane masa sirrikan mu? mahaifiyarta ta zauna damu ba da zuciya ɗaya ba sai don ta cutar damu gashi kuma tayi sanadiyar mutuwar mahaifina, sannan mahaifinta shine babban maƙiyi ne still aka sake turo Yushert domin ta kawo ƙarshen mu, good!..." tunowa yayi lokacin da sarki Raamud ya turo kuliya ta kawo masa takarda a ƙarshen rubutun yace a kula masa da Ɓingel.. A hankali Junaid ya furta "Ɓingel" yana jinjina kai, tareda faɗin "Yushert akwai abunda kike ɓoye mana, kuma asirinki ya tonu tinda har na gane cewa ke wacece, tambayar dana daɗe ina miki kika kasa amsa mun saboda bakida gaskiya..." ya ƙarasa maganar yana mai jin takaici a ransa, tunowa yayi da cewa su ɗin ƴan uwan juna ne, sannan ya tuno da mutuwar Uma Bara'at abun saiya ƙara ɗaure masa kai yace "what's going wrong, meyasa maƙiyiyata zata sadaukar da rayuwarta a kaina? shin meyasa maƙiyina zai tayani yin yaƙi? kenam maƙiyana sun koma masoyana?..." ya ƙarasa maganar yana sharar hawayen da suka zubo masa, miƙewa yayi yaje ya lalumo wayarsa wanda tin zuwansu ya kashe wayar ya ajiye, kunna wayar yayi ya duba cikin contact ɗinsa number mommy ya ƙira bugu ɗaya kuwa ta ɗauka a hanzarce dake lokacin tana kan sallaya ta idar da sallar lafula misalin ƙarfe 12 na dare tace "hello my son rabin raina ashe zamu sake ganawa da juna? nayi missed ɗinka my son yaushe zaka dawo?..." ata ɓangaren Junaid kuma zama yayi a bakin gado yace "it's okay my mom insha Allahu a cikin satin nan zan dawo gida, domin sai an yanka mana Visa..." Mommy tace "Allah ya dawo daku gida lafiya ashe Angel kam kwana ya ƙare ita da Rumana.." Junaid yace "Please ki bari saina dawo saboda yanzu kaina ne yake ciwo, ina Yushert?..." ya tambaya murya à sanyaye... Mommy tace "yanzu kam tana bacci a ɗakinta bata da lafiya, tinda muka kalli video waɗanda suka mutu aka nuno photon Bara'at daga nan aka nemi hankalinta aka rasa, bansani ba ko sun san juna ko kuma Bara'at ta cutar dasu bayan mu, kodai na kai mata wayar?..." rufe idonsa yayi sosai tsabar baƙin ciki yace "ok ki barta tayi baccin ta idan na dawo zamu yi magana..." Mommy ta amsa masa tana sharar hawaye da haka suka yanke wayar Junaid yayi wurgii da wayar yahau saman gado yana tunanin abubuwan da suke yawo masa a kayi... Mommy itama tashi tayi daga kan sallaya ta rage kayan jikinta ta sanya marasa nauyi sannan ta hau saman gadonta tana mai jimamin rashin Angel, sannan Bara'at ta tsaya mata arai ganin tsohon ciki a jikinta amma da haka aka kasheta, tayi matuƙar tausaya mata, tana cikin wannan tunanin har bacci ɓarawo yayi awun gaba da ita... ta ɓangaren Ayush itama a zaune take a tsakiyar gadonta ta naɗe sawayenta kamar mai cin tuwo, sai faman kuka take idon nan yayi jawur hatta fuskarta yayi jawur tsabar yawan kuka, Umanta ne take mata gizo! Babban tashin hankalin ma shine ganin Uma da tsohon ciki, wani irin ƙololuwar baƙin ciki ne ya tsaya mata arai, wani irin haɗiyar yawu tayi tana kuka tareda faɗin "an cutar dani sosai, an rabani da farin ciki na, an rabani da rayuka biyu mafi soyuwa a gareni wato mahaifiyata da kuma abunda ke cikinta nasan babu mai wannan aikin sai Junaid, domin burinsa shine yaga bayan iyayena, sannan yana iƙirarin zai nemo ɗiyarsu itama yaga bayanta, nasan idan har yasan nice ɗiyarsu nima kasheni zaiyi domin bashida tausayi da imani ko kaɗan acikin zuciyarsa, zuciyarsa ta gama ƙaiƙàshewa babu sauran imani a tattare dashi tinda har zai rufe ido ya kashe mata da tsohon ciki innalillahi wa inna ilaihi raju'un Allah ya isa na tsakani na dakai Junaid, bazan taɓa yafe maka ba, na tsaneka wallahi, tinda har ya iya kashe mace da cikinta to nima kasheni ba wani abu mai wahala bane agurinsa, ga mahaifina wanda yanzu babu cutarwa a zuciyarshi shima nasan kashe shi za'ayi, tabbas idan Junaid baiga bayan mu ba toh mutuwa yayi don haka zamana a gidan nan ya ƙare, babu amfanin zama guri ɗaya da maƙiya, duk da shiɗin ɗan uwa nane kuma jinina toh amma a yanzu na haramta wa kaina yin tarayya dasu domin su ɗin cikakkun maƙiyana ne, kiyi haƙuri mommy bazan iya zama daku ba, domin nasan wata rana zan iya sawa araina zan kashe ku to ke banason ki mutu amma dole zan kasheki saboda Junaid ya ɗanɗani kalar baƙin cikin dana shaƙa kafin shima mutuwar tazo kansa, Junaid wallahi wallahi sai naga bayanka, bazan ƙyaleshi ba, sai na ɗau fansar mutuwar mahaifiyata da cikin dake jikinta...." miƙewa tayi a fusace ta nufi wardrobe ɗinta ta ɗauko akwatinta ta tuttusa duk kayanta a ciki sannan ta zuge akwatin ta rufa mayafinta ta fice a ɗakin tana riƙe da jakar ta, har zata sauƙa down stairs ta fasa saida ta shiga ɗakin junaid ta fara yimasa bincike ko zataga wani abu mai muhimmanci, zuwa tayi ta tura wannan secret room cikin sa'a ta sameshi a buɗe, ta hanzarta ta shige ciki tareda kunna light ɗin ɗakin tsayawa tayi tana kallon photon mahaifiyarta da kuma mahaifinta tana zubda hawaye, nan danan ta fara bincika ɗakin tana kuka amma saidai abunda take bincikawa bata gani ba, domin tin bayan ɗauke takobin da akayi Junaid ya gano hakan yasa ya ɗauki littafin yaje ya bayar wa malam lawan domin ya adana masa, Ayush buga jikin gini ta fara yi tana kuka a fusace ta juyo tana wargaza shirgin ɗakin, su computer duk ta faffasa su, wasu abubuwansa masu amfani duk ta lalata masa su, fita tayi da gudu ta sauƙa falo kai tsaye kitchen ta nufa taje ta ɗauko galan petur ta dawo ɗakin Junaid ta wawwatsa petur sannan ta dawo falo nan ma ta watsa petur har su kitchen daga nan ta kunna gas saida ta kaishi ƙarshen number wutar yayi over da gudu ta ɗauki akwatinta ta buɗe falo tayi ficewarta, gudu take sosai har ta isa bakin gate cikin sanɗa ta buɗe gate ɗin ba tareda an jiyota ba, tayi ficewarta da gudu... Kitchen ɗin ne ya fara yin bonding daga nan wutan ya fita falo saiya haɗu da wayar nepa lokaci guda falon ya kama da wuta duk kujerun falo sunata ci da wuta, gobara gidan ya fara yi ta ko ina wuta yake badawa har zuwa room ɗin Junaid da Ayush gobara ne Mommy tana bacci ta fara jin warin petur ga wani baƙin hayaƙi da yake shugo mata, Kafin ta Ankare ƙofar ɗakinta ya fara ci da wuta, ganin abun yayi yawa kamar a mafarki ta buɗe idonta da sauri, ganin da gaske ne ƙaurin wuta takeji hakan yasa ta tashi a firgice ganin yanda ƙofar ɗakin yake ci da wuta yasa ta zaro ido waje tace "innalillahi wa inna ilaihi raju'un, wuta kuma? Ayushert Allah yasa dai tana lafiya, mun shiga uku..." tana rufe bakin saiga ƙofar ɗakin ya faɗo ta ciki nan danan gadon da take ya fara ci da wuta, ko ina ya kama da wuta, Mommy ɗaukar wayarta tayi ta nufi cikin toilet da gudu ta kulle sakamakon babu hanyar fita hatta falon ma ta ko ina wuta ya cinye, kuka take sosai tana ta jero addu'o'i tareda danna wayarta tana ƙiran number Junaid waran sau uku bai ɗauka ba, Dabara ne ya faɗo mata nan take tayi ƙiran gaggawa daga asibiti tana faɗin "dan Allah ku temaka gobara a gidana, ga can yarinya itama nasan ɗakinta ya kama da wuta emergency please...." ta katse ƙiran tana maida numfashi sama-sama sakamakon wani irin hayaƙi ne ya dabaibayeta ko numfashi bata iya fitarwa sai tari take tayi, ko gabanta bata iya gani tsabar hayaƙi lokaci guda hasken nepa ya ɗauke sai duhu daya biyo baya, Mommy daga wannan lokacin ta nemi hankalinta ta rasa, ga ƙofar toilet shima ya kama da wuta, tari take sosai kamar zata haɗiyi ranta har ta fara tarin aman jini, jini ne yake fita daga bakinta tsabar tari, sulalewa tayi ta faɗi ƙasi, ga wani irin ƙunan wuta da yake ratsa jikinta, ba abunda take furtawa sai sunan "Ayush! Ayush!! ku temake ta, Ayush kar ta mutu..." daga nan numfashi ya tsaya, Daiden lokacin da motar kawo agajin gaggawa ta iso tana bada jiniya, da gudun gaske suka shige da wayar feshin ruwa, Baba maigadi shima fitowa yayi ganin yanda gidan yake ci da wuta ne yasa ya fara ihu yana riƙe da kansa, domin ba'a tunanin za'a samu mutum mai rai a ciki saboda ta ko ina wuta ne yake ci..... ******* Junaid mafarkin da yake yi ne yasa baiji ƙiran da akeyi a wayarsa ba, yana cikin bacci bakinsa yana motsi a hankali yake furta "Yushert! Yushert!! Yushert!!! Please kar ki tsaneni, har yanzu ina kan sonki kuma bazan daina sonki ba har abada...." Ayush tana tsaye a gaban Junaid wanda bayansa wani ƙaton rami ne mai zurfin gaske, tana ta kwashewa da dariya haɗe da tafa hannayenta biyu tana shewa ga bindiga a hannunta, lokaci guda ta tsayar da dariyan tana wani irin kallo na ƙasƙanci tace "kayi kaɗan Junaid kai babban maƙiyi nane kuma bazan taɓa yafe maka akan laifin da ka aikata mun ba, rayuwarka a tafin hannuna yake, idan kaga na yafe maka toh kasheka nayi, kar kayi tunanin zan ƙyaleka, saina ɗau fansar jinin mahaifiyata da kuma abunda ke cikinta...." Junaid durƙusa wa yayi a gabanta yace "indai haka shine daidai agareki to Bismillah zaki iya kasheni yanzu, amma inaso ki sani soyayyarki bazata taɓa zamowa ƙiyayya ba acikin zuciyata inasonki Yaushert..." Kafin ya rufe baki ta harbeshi a kafaɗarsa ta kuma saita kayinsa ta harba cikin rashin sa'a iya bullet ɗaya ne a cikin bindigar, cikin takaici ta wurgar da bindigar gefe tana faɗin "kash naso ace na dagargaza maka ƙwaƙwalwa wallahi, idan ka furta mun kalmar so ji nake kamar ana ƙara rura mun wuta a cikin zuciyata, ganin kalmar nake tamkar mutuwata, na tsani kalmar soyayya sannan na tsani mai yin soyayya, Junaid mutuwarka hutu ne a gareni kuma samun nutsuwa ne a gareni..." Junaid yana riƙe da gurin da ta harbeshi yana kukan zuci idonsa akan Ayush wacce take tsaye akansa ko Annuri babu a fuskarta, idonta tsantsar ƙiyayya ne acikinsu buɗe baki tayi tace "kayi haƙuri ka gaida mun mahaifiyata da kuma ɗan uwana dake cikinta...." tana kaiwa nan tasa ƙafarta ta cankeshi yayi baya ya faɗa cikin wannan ƙaton rami mai zurfin gaske.... A ruɗe Junaid ya farka yana ihu tareda ambatar sunan "Yushertttt..." yana maida numfashi sama-sama ga gumin da ya wanke masa fuska, wani irin haɗiyar yawu yayi ga zazzaɓin da ya rufeshi ya ƙanƙame sai rawar sanyi yake tayi.... ****** A wannan daren misalin ƙarfe 2 da rabi Ayush tana tsaye a bakin gate ɗin gidan Doctor Hasheem tana ta faman bubbugawa tana kuka, jin motsin mutum yasa tayi shuru da yin kukan, ji tayi an tambaya cewa "waye ne?.." cikin sassanyar murya tace "Ni ce..." maigadi yace "ke wa?.." tace "Ayushert.." yace "ok ki jira toh mai gidan ya fito ya buɗe miki domin bazan mutu ni kaɗai ba wollah.." maigadi ne ya fara hura wusir da ƙarfi, cikin lokaci ƙalilan sai ga Doctor Hasheem ya fito cikin rigar bacci yace "wai meyake faruwa ne?.." cikin muryar jin bacci yake magana, Maigadi yace "daman Ogah wata mata ce take jiranka a waje..." cikin mamaki yace "wata mata kuma? a wannan daren? shin daga ina take?..." maigadi yace "a'ahhhh ban saniba aradu..." tafowa Doctor Hasheem yayi yazo ya buɗe gate baisha wahala waran ganeta ba saboda akwai hasken nepa ta wajen, gabansa ne yayi matuƙar faɗuwa cike da mamaki yake binta da kallo, baki na kakkarwa yace "Ayushert! ke daga ina?.." Fashewa tayi da matsanancin kuka..." girgiza kai yayi sannan yace "Junaid ko?.." yasa hannu ya jawota ciki sannan ya karɓi akwatin hannunta yajata suka nufi cikin gidan... A falo suka zauna tana kuka duk ta kwashe labarin ta gayawa Doctor Hasheem, jinjina kai Doctor Hasheem yayi sannan yace "kiyi haƙuri Ayushert haƙiƙa Junaid bai kyauta miki ba, bai kamata ya kashe miki iyaye ba, amma kema inaso ki sani komai ana binsa ne akan tsari duba da yanda kema iyayenki sukayi masa, shi wannan fansa ya ɗauka kema kinsan Junaid baya yafiya, amma duk da hakan yayi rashin imani gaskiya yasa hannu ya kashe mata mai ciki haihuwa yau ko gobe innalillahi wa inna ilaihi raju'un, dole kema bazaki yafe masa ba, banga laifinki ba Ayushert, ki ɗauki duk hukuncin daya dace ki ɗauka ina goyon bayanki, sannan zaki cigaba da zama damu acikin gidan nan..." Ayush tana kuka tace "a yanzu na ɗauki fansata akan mahaifiyarsa shima ya ɗanɗani raɗaɗin dana ɗanɗana..." ta ƙarasa maganar fuska a haɗe... Doctor Hasheem yana kallonta cikin rashin fahimta yace "ban gane mai kike nufi ba? kar kiyi kuskuren ɗaukan fansarki akan Mahaifiyarsa domin tayi miki halacci sosai a rayuwa kuma ita batada wata matsala..." Ayush juyowa tayi tana kallon Doctor Hasheem a fusace tace "kenam niɗin mahaifiyata matsala take dashi yasa ya ɗauki rayuwarta? mahaifiyata batada wani masoyi daya wuce Junaid, kullum maganar ta akan Junaid ne, mahaifiyata bata taɓa sa hannu ta mareni ba sai akan Junaid, shin sakayyar da zai mata kenam? uwa bata fi uwa ba, haka uba baifi uba ba, kamar yadda ya sheƙe mun mahaifiyata haka shima mahaifiyarsa yau za'a wayi gari itama ta sheƙa, sai mu zama marayu da gaske..." Doctor Hasheem haka yake bin Ayush da kallo gaba ɗaya ta sauya masa, ba Ayush ɗin daya sani a baya bane, yana tunanin a ransa cewa "Anya kuwa wannan Ayush ce? ina tunanin Aljana ce tazo mun a suffar Ayush...." daga nan ya fara tsorita da ita domin kalamanta sun girgiza shi, yana cikin wannan halin yaji ta ce "shin kana mamaki ko? kar ka damu ni ɗin ce Ayush, abunda akayi mun ne yasa zuciyata ƙaiƙashewa nima, kuma muje zuwa gaba shima Junaid saiya bar Duniyan nan, da hannuna zan kashe tsinanne la'ananne, ban taɓa yadda cewa soyayya takan zamo ƙiyayya ba sai yau kuma akaina..." jikin Doctor Hasheem ne yahau rawa daƙer ya buɗe baki yace "shin mai kika aikatawa mommy?..." kafin ya rufe bakinsa yaji wayarsa tana ring-ging a saman table ɗin tsakiyar falon, Hannunsa na kakkarwa ya ɗauki wayar ganin number hospital ne yasa ƙirjinsa bugawa da ƙarfin gaske yayi picking tareda karawa a kunne, ba tareda yayi magana ba yaji ance "Doctor Hasheem kayi saurin zuwa gidan Doctor Fateema gidanta duk ya cinye da wuta kuma mun rasata a cikin gidan, ko ina ya ƙone yayi ƙurmus, ga Oga Junaid baya ƙasan, kuma an hanamu ƙiransa mu sanar masa, dan Allah kai ɗin kazo ance mutum biyu ne a cikin gidan kuma bamu ga ko ɗaya ba acikinsu...." yana kaiwa nan ya katse ƙiran, Doctor Hasheem yar da wayar yayi ƙasi, idanuwansa sun ƙafe akan Ayush ji yake kansa yana juyawa, girgiza kai yayi a ruɗe ya tashi da gudu ya fice a falon,. a wannan daren yaje ya shige motarsa ya finciketa a ɗari ya nufi bakin gate, Maigadi ne ya fito da gudu jin ƙarar motar yazo ya buɗe masa gate, ya tafi da kayan baccin a jikinsa.... Bayan fitarsa Ayush fashewa tayi da matsanancin kuka mai cin rai tana faɗin "ki gafarce ni Mommy Dan Allah, kiyi haƙuriiiii...." kuka ne yaci ranta sosai, tana cikin rera kuka saiga Lailah ta fito tana sanye da rigar bacci zuwa gwiwarta, ganin Ayush yasa ta murtsuka idonta ko mafarki take ganin da gaske ne Ayush take gani ta sake baki tana kallonta.... *NACE BAAA YAU MA ZAN TAMBAYEKU HOW MARKET👋👋👋* 𝑡𝑦𝑝𝑖𝑛𝑔✍️ 𝗠𝗔𝗧𝗔𝗥 𝗗𝗔𝗠𝗨𝗦𝗔 the wife of a tiger🐅🐅🐅🐅 𝙼𝚊𝚕𝚕𝚊𝚔𝚒𝚗 𝙰𝚜𝚖𝚎𝚎𝚝𝚊𝚑 ✍️✍️ 𝙿𝚊𝚒𝚍 𝚋𝚘𝚘𝚔 𝚌𝚊𝚕𝚕 𝚘𝚛 𝚠𝚑𝚊𝚝𝚜𝙰𝚙𝚙 09065443871 *💫💫{{N W A}}💫💫* Book two C̶h̶a̶p̶t̶e̶r̶ 37 ➡️ 38 Doctor Hasheem a ɗari ya iso da motarsa yana zuwa ya buɗe ya fito ganin gidan yanata ci da wuta ne yasa zuciyarsa bugawa baki na kakkarwa ya furta "innalillahi wa inna ilaihi raju'un..." da gudu ya shige gidan ya ɗauki robar feshin ruwa ya ƙarasa shigewa ciki, ruwa ake badawa sosai har Allah yasa wutar ta mutu, Doctor Hasheem a hanzarce ya shiga ɗakin mommy yana dubata amma bai ganta ba, ga yanda tiririn wuta yake tashi, haka suke duba wa amma ba alamun mommy ga toilet duk ya cinye da wuta, girgiza kai Doctor Hasheem yayi sannan ya furta "mu rasata, wuta ta cinye ta shikenam Mommy..." wani zazzafan hawaye ne yake zuba masa, sai ji yayi ta bayansa ance "Doctor akwai yarinyar gidan a ɗakinta fah.." Doctor Hasheem kawar da kansa gefe yayi ba tareda ya kulashi ba ya juya yayi ficewarsa... ***** Lailah ce ta ƙaraso gurin da Ayush take tana tsaye tace "Ayushert meya kawo ki gidan nan a wannan daren?..". Ayush bata kulata ba ta cigaba da kukanta, ganin Lailah ta dameta da tambayoyi yasa Ayush miƙewa tana faɗin "idan kinaso na bar muku gida saina tafi ai koh.." Lailah ta zaro Ido waje tace "me yayi zafi haka, cigaba da zamanki bani na kawoki ba, idan tayi tsami ma ji.." Lailah juyawa tayi ta nufi waran frig ta buɗe ta ɗauki Apple da farro ta koma ɗakinta daman yunwa ne ya fito da ita... Ayush tayi waran awa biyu tana zaune bata rintsa ba, can saiga Doctor Hasheem ya shugo cikin damuwa yana tafiya kamar babu laka a jikinsa, zuwa gaban Ayush yayi ya tsaya yana faɗin "shin kin kyautawa kanki? yanzu kinji daɗi ko mommy ta ƙone tayi ƙurmus babu alamun gawarta, yanzu kin ji daɗi?..." Ayush bata bashi amsa ba itama miƙewa tayi ta ɗauki akwatinta tayi hanyar fita, Doctor yace "ina zaki je kuma?.." tace "zanje gurin da ba takurawa, na zaɓi nayi rayuwata ni kaɗai..." Doctor Hasheem yace "amma ki sani idan Junaid yaji labarin ke kika ƙone gidansu bazai barki ba, kizo ki zauna damu anan gidan insha Allahu zan rufa miki asiri, shima Junaid zan san abunda zan gaya masa wanda bazai tuhumeki ba, amma muddin aka san cewa kece kika kashe Doctor Fateema ta hanyar wutar petur toh bakin mutane ma kaɗai ya isheki, za'ayi miki abunda akayi wa mahaifiyarki kema ki koma jeji da zama, idan kin zaɓi haka shikenam..." Ayush juyowa tayi tazo gaban Doctor tana cewa "zan zauna dakai saboda gudun abunda zan tarar, amma bawai don ina tsoron Junaid ba, so nake na tinkare shi gaba da gaba, zan nuna masa cewa nima jar wuya ce..." Doctor Hasheem yana tsaye baice mata komai ba, ta kuma cewa "inaso ka ƙira Junaid a yanzun nan ka sanar masa mutuwar mahaifiyarsa ya fara jin raɗaɗi a zuciyarsa kafin a wayi gari..." Girgiza kai Doctor yayi yace "bazan iya sanar masa mutuwar mahaifiyarsa a halin yanzu ba, amma zan sanar masa cewa anayi masa ƙiran gaggawa! wannan ma zanyi ne saboda tsananin soyayyar ki..." Ayush jinjina kai tayi sannan tace "Nagode.." A lokacin kuwa Doctor Hasheem ya ƙira wayan Junaid bugu ɗaya kuwa ya ɗaga domin so yake yaga ƙiran wani daga Nigeria, domin yayita ƙiran wayan mommy a kashe bayan yaga missed call ɗinta, Junaid ne ya fara yin magana yana faɗin "hello Doctor Hasheem lafiya kuwa? meyake faruwa ne naga ƙiran mommy misalin ƙarfe 1 har three missed call, nabi ƙiran kuma switch up kaima kuma ga ƙiranka yanzu ƙarfe 3, Allah yasa dai lafiya..." Duk maganar da Junaid yake yi Ayush tana jinsa domin a handspring yake, Doctor Hasheem kamar bazaiyi magana ba, tsabar fargaba da kuma baisan mezai gaya masa ba, maganar da Ayush tasa ya gaya masa yanada nauyi bazai iya gaya ba, Junaid ne ya ƙara yin magana yace "lafiya kuwa Doctor Hasheem, yanaji kayi shuru..." Ayush ganin Doctor Hasheem bashida niyar yin magana yasa ta karɓi wayar cikin yanayin fushi saida ta daidaita kanta tukun tayi magana tana faɗin "Yaya Junaidddd..." cikin kuka ta ƙira sunansa da nuna damuwa. Gaban Junaid ne yayi mungun bugawa jin muryar Ayush, sai kuma ya tuno da mafarkin da yayi akanta.. tana kuka tace "Gobara ya tashi a gidan mu kuma mommy tana ciki mun kasa ceton rayuwarta, nima daƙer na kuɓuce, na kasa ceton mommy dake ɗakinta a kulle yake ta ciki, gida ya cinye ƙurmus, yanzu haka ina gidan Doctor Hasheem na rasa ina zanje, amma mun ƙira masu temakon gaggawa..." ta ƙarasa maganar tana haɗe fuska da gira... Junaid ƙamewa yayi guri ɗaya ya kasa motsawa daga baya jikinsa yahau yin ɓari, wayarsa ta kuɓuce daga hannunsa ta faɗo ƙasi, numfashinsa ne yake shirin ɗagewa.. Ayush murmushi tayi bayan ta katse wayar tace "a yanzu kalamai na tamkar mashi yake, kuma nayi nasarar cakar cikin zuciyarsa, a lokacin da ya kashe mun mahaifiyata babu imani a tattare dashi, toh nima a yanzu babu wannan imanin, kuma saiya girbi abunda ya shuka..." ta ƙarasa maganar tana sharar hawaye tana riƙe da akwatinta tace "aina zan zauna?..." Doctor Hasheem kwata-kwata lamarin Ayush ya fara bashi tsoro, gaba yayi yace "biyoni.." haka ta bi bayansa har yakai ta ɗakin da zata zauna, ɗakin kusa da ɗakinsa... Duk tattaunawar da sukayi Lailah tana laɓe tana jinsu, gaba ɗaya ta girgiza dajin wannan batun, a hankali ta furta "whattt, Ayush kin ƙona mommy ta hanyar dasa gobara? Innalillahi wa inna ilaihi raju'un, duk rashin imani na bazan iya wannan babban kuskure ba, tabbas biri yayi kama da mutum daman bada zuciya ɗaya take zaune dasu ba, daman ance ka kiyayi mai shuru-shuru domin wata rana zaiyi abunda ƙwaƙwalwa bazai iya ɗauka ba, hmm wai mace mai haƙuri gashi yanzu mommy kin mutu ata sanadiyar mace mai haƙuri, kuma Insha Allahu Ayush saina tona miki asiri bazan bari ayi wannan aika-aika a gabana na ƙyale ba..." Lailah ta ƙarasa maganar tana zubda hawaye ta shige ɗakinta, mutuwar mommy ba ƙaramin girgiza ta yayi ba... Ata ɓangaren Junaid kuwa da gudun gaske yayo bakin gate yana ihu tareda faɗin "My mom! My mom!! zata mutu ku temaka mun Please, banaso na rasata ita kaɗai nake da a duniyan nan, ita kaɗai ce gata na Please open the gate...." Security ne suka riƙe shi sosai, shi kuwa ƙoƙarinsa shine ya fice yaje airport, ihun da yake yi ne yajawo hankulan sojojin hotel ɗin duk suka fiffito, Sai rarrashinsa suke amma baya sauraronsu, shi dai abunda yake ambato shine mommy! Mommy!! Mommy!!! kunnuwansa gaba ɗaya sun toshe balle yaji rarrashi, gaba ɗaya ya rikice har saida aka masa allurar samun nutsuwa na sojoji tukun ya shiga hankalinsa.. Da sassafe bayan sallar asuba aka bar Junaid ya taho airport da jakarsa, cikin sa'a kuwa a lokacin jirgin zai tashi zuwa Nigeria... ****** Da safe mutane ne a cike tam a ƙofar gidan mommy, ga yanda wuta yayi ta'adi komai yayi ƙurmus a gidan, gidan yayi baƙi ƙirin, masu video sunayi masu ɗaukan photon gidan sunayi, kafin daga baya saiga ƴan jarida da masu rahotanni kowa yana son jin yanda akayi gidan ya ƙone da Doctor Fateema da kuma yarinyar gidan... Malam Lawan shima yana cikin mutanen hankalinsa ba ƙaramin tashi yayi ba, wannan al'amarin duk ya zagaya garin Abuja part to part... Kafin kace mai har an buga jaridu da kuma masu magana a television, magana duk ya zagaya social media... ____________Ayush tana zaune a bakin gadonta a gidan Doctor Hasheem tayi tagumi sai zubda hawaye take, a haka Doctor ya shugo ya tarar da ita, a cikin damuwa ya shugo yana faɗin "Ayush yanzu maganar mutuwar mommy ya bazu ta ko ina, kuma ana tunanin kema kina cikin gidan wutar tayi gobara, idan har aka san kina raye to zargin zai koma kanki ne, kuma hukuma bazata ƙyaleki ba, shin kinsan wacece Doctor Fateema kuwa? kinyi kuskure Ayushert, gashi kin sanarwa Junaid cewa kina raye a yayin da kuma mutane suke maganar har da ke wutar ta kama..." Doctor Hasheem kasa ƙarasa maganar yayi ya dafe goshinsa yana mai jin takaicin abunda ya faru ga kuma indai aka san Ayush tana nan shikenam dole za'a tuhumeta.... Ayush ƙanƙame jikinta tayi tsabar sanyin da take ji, bakinta har wani kakkarwa yake tana kuka tace "ai daman nasan dole za'a tuhumeni, kuma dole zan amsa laifi na duk da nasan nima kasheni za'ayi, babu wata mafita a gareni..." Doctor Hasheem yana kallonta cike da tausayawa yace "Ayush kuskure na biyu da kika aikata shine sanar da Junaid da kikayi, kinga shi yasan kina raye, amma in badan haka ba ni zansan yanda za'ayi baza asan kina raye ba, niyata shine na yanka miki visa kibar ƙasar nan gaba ɗaya, ni zan ɗauki ɗawainiyar ki har ƙarshen rayuwarki, amma yanzu idan kika tafi dole Junaid zaiyi zargin wani abu..." Ayush gaba ɗaya ta rasa yanda zatayi, ga wani irin zazzaɓin da take ji... Doctor Hasheem ne ya miƙa mata hannu yace "taso muje kiyi breakfast nasan kina jin yunwa..." Ayush kallon tafin hannunsa tayi ta kawar da kanta gefe ba tareda ta miƙa masa hannu ba tace "inaso a kawo mun nan..." shima kawar da hannunsa yayi yace "Okay don't worry, wait for me..." juyawa yayi ya fice daga ɗakin... yana fita ya nufi kitchen anan ya tarar da Lailah tana shirin fitowa da plate ɗin abinci a hannunta, tana kuka, yana ganinta yace "ke kuma fa keda waye kike kuka?.." Da damuwa a fuskar Lailah tace "mommy Junaid ta mutu, gashi anata nuna wa a tv, gidanta duk ya ƙone..." ta ƙarasa maganar tana kuka shaɓe-shaɓe. Doctor Hasheem yace "kiyi haƙuri ƙanwata gobara ne ya tashi a gidan basu saniba, dake bacci suke yi..." taɓe fuska Lailah tayi gira a haɗe tana jinjina kai tace "toh amma meya kawo Ayush gidan nan?.." har saida zuciyar Doctor ya buga jin wannan tambayar na Lailah, yana sosa ƙeya yace "Ayush daƙer ta kuɓuce ta gudo nan gidan sakamakon rasa inda zata je..." ta sake cewa "toh Amma Yaya ai naji mutane suna ta faɗin har da ita ta ƙone.." Yace "eh mutane sunyi tunanin harda ita.." harararsa tayi ba tareda ya saniba tace "toh ai saita fito ta bayyana kanta inba rashin gaskiya ba" Doctor Hasheem ya kalle ta yace "ke bakida hankali ne, idan ta bayyana kanta ai zargin mutane zai koma kanta ne..." turo baki Lailah tayi tace "Ohh hooo na gane..." a cikin zuciyarta kuwa cewa tayi "wallahi Yaya ka koyi munafurci yanzu, kuma ba ƙaramin raina mun wayo kayi ba, kuma saina tonawa Ayush asiri ehen ai nayi recorded duk maganganun da tayi...." Shi kuwa Doctor Hasheem tinin ya shige cikin kitchen saboda kar Lailah ta sake jifansa da wata tambayar again... Itama ɗakinta ta wuce da abincinta tana ta danne-dannen waya.. *Bayan Awa Biyar5* Junaid ne ya iso ƙofar gidansu da motar haya da ta ɗauko shi daga airport, Da gudun gaske ya fito daga cikin motar ya shige gidan, ganin ko ina ya ƙone yasa shi ganin dishi-dishi saida yasa hannu yana murtsike idonsa ko mafarki yake ganin a zahiri yake ganin al'amarin ne yasa ya rufa da gudu yayi cikin ɗakin da gudu duk ginin ya rurrushe yayi baƙi ƙirin, tsayawa yayi kamar wani zararre ga hajijiyan da yake shirin ɗaukarsa, bai ma lura da mutanen dake wajen ba, baya yayi zai faɗi malam lawan yayi saurin riƙo shi yana faɗin "kai Junaid ka dawo hayyacinka mana, ka nutsu kaji abunda zan gaya maka..." Shi kuwa Junaid a lokacin ma har ya sume a gurin... mutanen wajen sun ragu sosai, a yanzun mutanen ba yawa daga malam lawan ne sai Baba maigadi sai kuma maƙobta, duk an gama ɗaukan rahotanni sun tafi... Malam lawan yana tafe da Junaid a hankali har sukazo wajen motarsa ya kwantarshi a kujerar baya, yace da Baba maigadi shima yazo ya shiga su tafi gidansa, haka malam lawan shima ya shiga yana jan motar a nutse suka nufi gidansa... Duk wannan hidimar da akeyi kar ku manta Damusa yana tafe a bayan Junaid, kasancewar Malam Lawan yasan da zaman Damusan bai wani tsorita ba, haka shima ya saka shi a cikin motar, amma sauran mutanen gurin duk sun gudu ganin Damusan... *After 3 months* Mommy tana ƙwance akan wani katafaren gado, tana ta shan baccin ta bayan farfaɗowa daga doguwar suma, farkawar ta daga bacci yake da wuya ta soma buɗe eyes ɗinta a hankali, wani irin haske take gani da sauri tasa hannu ta rufe idonta tana ƙoƙarin tashi zaune, ji tayi ance "kodai na tayaki tasar dake?..." da sauri mommy ta ƙarasa tashi zaune ta waiwayo tana kallon wanda yayi mata maganar, Ganin mutumin yasa ƙirjinta bugawa da ƙarfin gaske, leɓɓen bakinta ne suka ɗau rawa murya na kakkarwa tace "shin mafarki nake yi ne ko kuma na mutu da gasken? nidai nasan gidana ya kama da wuta kuma na ƙone a cikin wutan, mijina na iso yanda kake, daman ance duniya ba matabbata bane, yau gani ga mijina wanda na rasa shi tin shekara da shekaru, mijina shin yanzun a aljanna muke ne?..." ta ƙarasa maganar tana kuka, ta zubawa wanda take kallo ido... Sarki Raamud dake zaune a bakin gadon da take ne ya kalli Narasimha yace "Baba Narasimha har yanzu ƙwaƙwalwarta bai gama yin saiti ba, a ƙara duba ta mana...." Mommy tana murmushi idonta akan sarki Raamud ita bata ma lura da Narasimha ba saida ta ɗan waiwaya tukun suka haɗa ido huɗu, ja da baya mommy tayi da sauri ta zaro ido waje kamar zatayi kuka tace "mijina wannan shine mala'ikan da yake gadinka? amma inadai kana samun rahama koh, wannan wani mala'ikan ne?..." Sarki Raamud ne ya dubeta yace "Amm ki kwantar da hankalinki ba mutuwa kikayi ba, har yanzu kina nan a duniya, wannan ba mala'ika bane ba shima a doron duniya yake..." Mommy tana kallonsa ido cikin ido tace "daman kaima baka mutu ba?..." Sarki Raamud shima hawaye ne suka fara cicciko masa saboda shima ya tuna da matarsa kuma sarauniyarsa Bara'at daƙer ya buɗe baki yace "ba nine mijinki ba, ni ɗan uwan mijinki ne..." Mommy tana kuka tace "bangane mai kake nufi ba, kana nufin kace kaiɗin ba mijina bane? toh idan ka manta dani ai bazaka manta da ɗan ka Junaid ba koh?..." Sarki Raamud bazai iya bata amsa ba sakamakon kuka da ya kuɓuto masa, ita ɗin ma kukan take... Narasimha ganin baza su iya bawa juna haƙuri ba yasa yazo har gabansu yasa sukayi shuru ko wannensu ya maida hankalinsa kansa, Narasimha yana kallon mommy yace "kiyi haƙuri baiwar Allah wannan ba shine mijinki ba, amma kuma ɗan uwan mijinki ne wato sarki Raamud, wannan shine mutumin da kike jin labarinsa a ko'ina kuma shine a baya yake cutar miki da yaronki Junaid, Amma yanzu ya rigada ya shiryu...." Hankalin mommy ne ya fara dawowa jikinta anan ta fara tunanin ganin sarki Raamud da tayi a television lokacin da aka kamo shi, tana kuka ta nuna sarki Raamud da yatsa tace "daman kaine sarki Raamud? Kuma ɗan uwan mijina?..." Sarki Raamud jinjina kai yayi yana kallonta,. Narasimha ne yace "kar kiyi mamaki domin yanzu zan baki tarihin rayuwar mijinki da kuma wannan sarki Raamud..." Mommy juyowa tayi tana kallonsa, Anan ya fara kora mata jawabai yana bata labari tin daga kakanun kakanun su sarki Raamud..." ******* Shi kuwa Junaid shima yana zaune akan gado, har wannan lokacin yana gidan malam lawan sakamakon rashin lafiyan da yasha domin har yanzu baya iya cin komai kullum a cikin tunanin Mommy yake, gaba ɗaya ya fita hayyacinsa duk yabi ya rarrame yayi fari sol dashi kamar ba jini a jikinsa, Damusa yana ƙwance a ƙasin gadon da Junaid yake shima ba wargi a tattare dashi ganin Junaid a halin da yake ciki, Malam Lawan ne ya shugo da sallama a bakinsa, daƙer Junaid ya iya amsawa, murmushi malam lawan yayi yana faɗin "Alhamdulillah yanzu ka fara samun sauƙi Junaid tinda yanzu kana iya amsa sallama.." zuwa yayi ya zauna a bakin gadon shima ya riƙo hannun Junaid yace "Junaid Dan Allah ka zamo mai tawakkali a rayuwa, nasan kana jin raɗaɗin ciwon rashin mahaifiyarka da kuma Ayushert amma haƙuri zakayi, akwai yaran da iyayensu suka mutu suka barsu amma haka suke shan gwagwarmayar rayuwa, kaima kayi haƙuri, mahaifiyarka addu'a take buƙata a halin yanzu...." Junaid tinda malam ya fara magana yake kallonsa har zuwa yanzu idonsa akan malam daƙer yake motsi da bakinsa yace "yaushe Yushert ta mutu?..." Malam yace "eh mana har da ita wutar ta cinye..." Junaid girgiza kai yayi sannan yace "Yushert tana nan a raye, ita ta sanar mun mutuwar mahaifiyata a lokacin da abun ya faru.." Gaban malam ne ya yanke yace "Ayshert tana raye daman?..." tashi Junaid yayi yana faɗin "Malam inaso ka rakani gidan Doctor Hasheem..." ya ƙarasa maganar yana zaro jallabiya a jikin wardrobe ɗin ɗakin, ya sanya shi domin iya 3quater ne a jikinsa sai singlet, Shima Malam tashi yayi yana mamakin ya za'ayi ace Ayushert tana raye kuma bata nemeni ba ko shi Junaid?..." bin bayan Junaid yayi zasu fita, Damusa ne shima ya miƙe zai bisu Junaid ya waiwayo yace "Sujjur zauna zan dawo yanzu.." Damusa ya koma ya ƙwanta abunsa.... *MASHA ALLAH FATAN KUNA JIN DAƊIN LITTAFIN THE WIFE OF A TIGER* *TO BE CONTINUE NEXT.... 𝑡𝑦𝑝𝑖𝑛𝑔✍️ 𝗠𝗔𝗧𝗔𝗥 𝗗𝗔𝗠𝗨𝗦𝗔 the wife of a tiger🐅🐅🐅🐅 𝙼𝚊𝚕𝚕𝚊𝚔𝚒𝚗 𝙰𝚜𝚖𝚎𝚎𝚝𝚊𝚑 ✍️✍️ 𝙿𝚊𝚒𝚍 𝚋𝚘𝚘𝚔 𝚌𝚊𝚕𝚕 𝚘𝚛 𝚠𝚑𝚊𝚝𝚜𝙰𝚙𝚙 09065443871 *💫💫{{N W A}}💫💫* Book two C̶h̶a̶p̶t̶e̶r̶ 39 ➡️40 Narasimha a labarin da ya bawa mommy kam ba wanda ya tsallake hatta silar warkewar Junaid bai ɓoye mata cewa a silar Ayush ya warke ba... Mommy kuka take sosai tace "Allah Sarki Ayushert daman wannan zoben data cire a cibiyarta shine maganin warakar Junaid? ta bayar da rayuwarta akansa, tasha jinya sosai, amma silar warkewar ta ai kaine, Muna godiya sosai..." tana kallon Narasimha cike da farin ciki.. Narasimha yace "basai kin gode mun ba saboda su ɗin sun kasance jinin sarauta ne, kuma kakansu sarki Zaid mutumin kirki ne, ko dan shi zan temaki ahalinsa..." Mommy tana girgiza kai cike da damuwa tace "Allah Sarki Bara'atu munyi mata mummunan fassara ashe itama ba'a son ranta tayi haka ba, anyi amfani da ita ne ta hanyar asiri, nayi tunanin Junaid ne ya kasheta ashe ita ta bada rayuwarta akansa, Allah ya gafarta mata, kuma Allah ne yasa mijina zai mutu ta hanyar nan, idan ajali yayi ƙira babu wanda ya isa ya tsayar da mutum, Allah ya jiƙanka mijinaaaa..." ta ƙarasa maganar tareda fashewa da wani irin matsanancin kuka... Sarki Raamud shima yana zaune yana zubda hawaye cikin rarrashi yace da mommy "kiyi haƙuri Fateema duk laifi nane, ni nayi sanadiyar mutuwar ɗan uwana kuma mijinki, sannan inaso na nemi yafiyar Junaid akan abubuwan da na aikata masa na zalunce shi saboda son zuciyata, Mayushert ɗiyata ce amma itama na cutar da rayuwarta ta hanyar dasa mata abunda zai cutar da ita acikin cibiyarta, sauran kaɗan na rasata, dan Allah ku gafarce ni, ku yafe mun Fateema.." Itama ɗagowa tayi tana kuka idonta akansa tace "kar ka damu Sarki mun yafe maka kuma Insha Allahu Allah zai yafe maka, ka cigaba da addu'a tinda Allah yaga zuciyarka, kazo ka rungumi ƴaƴanka hannu bibbiyu, suma zasu ji daɗin kasancewa tareda kai a matsayin mahaifi..." Sarki Raamud share hawayensa yayi yana murmushin farin ciki tabbas yaji daɗin kalaman mommy, domin har cikin zuciyarsa ta ratsa, ɗagowa yayi yana kallonta yace "Nagode sosai mai kyakkyawar zuciya, haƙiƙa Junaid da Mayushert sunyi dacen uwa ta gari, Amma sai daiii..." ya ƙarasa maganar tareda shiga wani irin yanayi na baƙin ciki yace "haƙiƙannin gaskiya banji daɗin abunda Mayushert tayi miki ba, gobarar da ya tashi a gidanki ba haka kawai ya tashi ba, Narasimha yana gani yanda akayi kuma ya sanar mun, toh amma ni bazan ɓoye miki ba domin idan har kika ji daga baya ranki zai sosu matuƙa, toh amma ni nafison na gaya miki abunda ɗiyata ta aikata miki ba maganar ɓoye-ɓoye, wato Mayushert ita da hannunta ta tayar da gobara a gidanki tana so ki ƙone sakamakon tana tunanin Junaid ne ya kashe mata mahaifiya...." Sarki Raamud ya ƙarasa maganar yana kallon mommy cikin tausayawa, Mommy bata nuna alamar baƙin ciki ba ko kaɗan sai murmushin da tasau tana girgiza kai tace "Allah Sarki yarinta kenam, tana so nima ta kashe ni ne saboda Junaid ya ɗanɗani baƙin ciki shima kuma banga laifinta ba ko kaɗan wallahi, Allah Sarki ƴata Ayush tausayi take bani wallahi, ashe ma jinina ne ita ɗin..." Babu wani alamar damuwa a fuskarta. Sarki Raamud yace "kar kice haka Fateema domin Ayush butulci tayi miki..." bai ƙarasa maganar bama ta katse shi da cewa "laaa kar kayi kuskuren faɗin haka domin nasan har yanzu ina cikin zuciyar Ayush, Ayush tanada kyakkyawar zuciya kuma ƴar baiwa ce, banaso ana aibata ta a gabana, domin duk wanda ya kushe Ayush toh maƙiyi nane ba masoyi ba saboda ta kasance jinin jikina ne..." Sarki Raamud shima murmushi yayi yana sauraronta, ta cigaba da cewa "Ayush burinta Junaid ya shiga halin ƙunci a halin yanzu domin suna tunanin na mutu, toh kuwa zan cika mata burin natan, saboda haka bazan koma yanda suke ba har sai Ayush da Junaid sun daidaita kansu domin su ɗin ma'aurata ne, zan cigaba da zama a cikin wannan masarautar mai tarin albarka..." Sarki Raamud yace "toh shikenam Insha Allahu za'a nemo miki mata waɗanda zasu tayaki zama kuma suyi miki duk wasu ayyukan da kike buƙata..." Mommy murmushi tayi sannan ta sunkuyar da kanta ƙasa tace "Nagode Sarki.." Sarki Raamud shima murmushin yake ya kalli sama yace "mu godewa Allah, nima yanzu banida wata matsala, domin an rigada an wanke ni a idon jama'a, duk laifukan da nayi an maida su kan Munafurr wanda ya sheƙa tintinin, duk ba kowa ne yayi mun wannan ƙoƙarin ba sai Junaid, kafin ya koma Nigeria shi yayi rubutu ya turawa shuwagabanni hukumomi, kuma an tabbatar bani aka yaƙa ba hasali ma har da ni muka yaƙi babban annoban, yanzu dai nayi free, kuma wannan masarautar za'a ƙara tsara shi ne, a sako mutane a cikinta waɗanda zasu na hidimar aiki, da kuma fadawa, zan sauƙa akan mulkin nan Insha Allahu Prince Junaid da Princess Mayushert sune zasu cigaba da mulki a acikin masarautar nan...." Mommy ta sauƙar da ajiyar zuciya tana kallon sarki Raamud tace "toh kenam kai baza kayi Aure ba? naga akwai part-part ɗin ɗakuna acikin masarautar nan sun kai 10 kuma manya-manya..." Murmushi sarki Raamud yayi sannan yace "ehhh acikin part ɗin ɗakunan zan zaɓi ɗaya na zauna a ciki kafin rai yayi halinsa ba tareda matar Aure ba, domin ni na rigada na yanke cewar bazanyi Aure ba har ƙarshen rayuwata..." ya ƙarasa maganar yana kallon mommy, itama ya tambayeta cewar "ina kema a cikin masarautar nan zaki cigaba da zama da yaranki?.." Murmushi tasau tace "eh kamar yanda kaima kace haka nima zan zaɓi ɗaki ɗaya na zauna ni kaɗai, daman tinda mijina ya rasu na yanke cewa ba wanda zan Aura..." Narasimha duk tattaunawar da sukeyi a junansu yana jinsu, yayi gyaran murya sannan yace "idan kun gama shiriritar takun ni zan koma yanda na fito kafin na sake dawowa..." Sarki Raamud ne yayi saurin miƙewa sannan ya durƙusa ƙasi tareda haɗe hannayensa biyu yana roƙan Narasimha akan ya zauna dasu, "Dan Allah Baba Narasimha kayi haƙuri ka cigaba da zama a tare da mu, inason ka kasance tareda mu domin zakana bamu duk wata kariya kuma zaka warkar mana da jinyar da ya gagare mu indai bana ajali ba, dan Allah..." Narasimha yace "a'ah Raamud bazan iya zaman duniya ba, tafiya zanyi can wajen da nake zaune.." Sarki Raamud hawaye ne suka cicciko masa yace "Baba Narasimha ka tuna fa mahaifina ya baka amanar mu, kar ka tafi ka barmu tinda yanzu ruhinka ya komo jikinka da temakon Damusa..." Jikin Narasimha ne yayi sanyi yace "toh shikenam zan zauna daku...." Daman akwai ɗakin Narasimha da ban wanda aka tanadar masa, ɗakin da ba kowa ne yake shigansa ba... Sarki Raamud yayi farin cikin jin abunda Narasimha ya faɗa yace "Nagode Narasimha amma yanzu inaso kayi mun wata alfarma ɗaya..." Narasimha yace "meye matsalar?.." Sarki Raamud yace "Damusa nake so ya zauna dani, na tabbata a can Nigeria duk wanda yaga Damusa zaiyi ƙoƙarin tserewa ne, kuma kaga Damusan daman na masarauta ne, bazaiji daɗin zama a wajen Junaid ba.." Narasimha yace "wannan gaskiya ne, zaman Damusa Sujjur a cikin masarauta shine zaman lafiyansa domin shi ba kamar sauran Damusa bane, abincinsa da ban ne, don haka yanzu zanje na ɗauko Damusa Sujjur..." Narasimha yana kaiwa nan ya ɓace ɓatt... ******** Lailah tana zaune a harabar gidansu akan kujerar roba tana waya tana faɗin "kinga Maimoon ya zaki cemun kinada ciki? bayan sau ɗaya akayi amfani dake..." Ata ɓangaren Maimoon kuwa cewa tayi "Laila nidai na gaya miki shi Allah babu ruwansa da sau ɗaya akayi, ciki ne Allah ya bani bansan ya zanyi ba, kuma muddin Daddy nah yaji wallahi saiya ɗauki ƙwakkwaran hukunci, gashi yanzu cikin har ya soma fitowa amma ban yadda an gane ba har yanzu..." Lailah tace "yanzu cikin zaije wata nawa?.." Maimoon tana kuka tace "yanzu fah yana shirin shiga wata na Bakwai.." Lailah ta zabura tace "innalillahi wa inna ilaihi raju'un, Maimoon ciki ai ya girma, kin kusan haihuwa, toh yanzu ya za'ayi? wallahi kinyi sakaci Maimoon meyasa tin da baki sanar mun ba sai yanzu, ai da an zubar yanzu kuwa babu halin zubar wa..." Maimoon tana kuka tace "toh yazanyi, meye mafita.." Lailah juyowa tayi zatayi magana kwatsam sai taga Junaid yana tsaye ata bayanta, shi kuma Malam Lawan yana cikin motarsa bai sauƙo ba, Gaban Lailah ne ya yanke ta dafa ƙirjinta tace "innalillahi wa inna ilaihi raju'un nashiga uku.." Junaid yace "kinga babu ruwana da tattaunawar da kikeyi da munafukan ƙawayenki, shin ina Yushert?.." Lailah hannunta na rawa ta nuna cikin falo tace "tana ciki.." juyawa yayi ya nufi ciki, Lailah ce ta kara wayarta a kunne tace "kinga Maimoon zamuyi magana daga baya..." ta katse ƙiran tabi bayan Junaid da gudu... A ɓangaren Maimoon kuma bayan ta sauƙe wayarta tana kuka sai ji tayi an turo ƙofa, da sauri ta ɗago tana kallon Ammy wacce ta shugo da hawaye shaɓe-shaɓe akan fuskarta, Maimoon a tsorace tace "Ammy meyasa kike kuka?.." Ammy ta taho gurin Maimoon tana kuka tasa hannu ta cire dogon hijab ɗin Maimoon, saiga tumbin ciki har ya fito sosai, Bazaka taɓa gane Maimoon tanada ciki ba indai ba lura kayi sosai ba, saboda kullum a cikin ɗakinta take, bata yadda taje falo saidai Ammy ta kawo mata abinci kuma kullum da hijabi a jikinta, Anyi Anyi da ita amma taƙi fitowa cikin mutane, hatta mahaifinta shima yayi har ya gaji sun ƙyaleta.. Ammy ganin ciki a jikin Maimoon yasa taja baya da sauri tareda dafe ƙirjinta tace "nashiga uku Maimoonnn? yanzu abunda yake tare dake kenam? kike ɓoye mana? yanzun ma ji nayi kina waya da Lailah shiyasa na sani amma inbadan haka ba saidai idan naƙuda ne ya tarar dake, nashiga uku nah, yanzu har ciki yayi wata bakwai a jikinki ban saniba Maimoon?..." Maimoon tana kuka tareda faɗin "dan Allah Ammy kuyi haƙuri ku gafarce ni, nasan nayi kuskure da ban sanar muku ba, inajin tsoron Daddy, bansan ya zanyi ba Ammy..." Ammy itama kukan take tace "Maimoon waye ne ya miki ciki?..." Shuru tayi Maimoon ta gagara bada amsa sai kuka, Ammy ta sake yin magana tace "magana nake miki Maimoon ki ban amsa mana.." Maimoon murya na kakkarwa tace "nima ban saniba Ammy, bansan inada ciki ba sai da naga ya fito.." Ammy tace "kodai mutanen da suka sace ki ne suka ɗirka miki cikin?..". Maimoon tana kuka tace "ehh sune.." Ammy cikin damuwa tace "Insha Allahu za'a ɗauki mataki akansu" daganan Ammy tayi waje cikin ɓacin rai.. ****** Junaid yana shiga cikin falo ya tarar da Ayush zaune tana fuskantar plasman ita kaɗai, juyowa tayi ta kalli wanda ya shugo ganin Junaid yasa ta miƙe tsaye da sauri tana kallonsa, saiga Lailah itama ta shugo, kalle kalle suke yiwa junansu ba wanda ya kula kowa acikinsu, daga baya saiga malam lawan shima ya shugo ganin Ayush yasa shi faɗin "Ayshert daman kina nan a raye? taya kika bar gidan nan?.." Ayush fashewa tayi da kuka ba tareda tace musu komai ba, Junaid ne yazo gabanta ya tsaya suna facing juna yace "ki gaya mun gaskiya taya akayi gidan mu ya kama da wuta kuma mahaifiyata tana ciki?.." wani irin kallo Ayush ta watsawa Junaid tace "wannan wani irin tambaya ne? shin inda nima na ƙone a ciki zaka samu kayi mun irin wannan tambaya ne?.." Junaid kallonta yake cike da mamaki bai taɓa tunanin Ayush zata iya bashi wannan amsar ba, yace "shin kina farin cikin mutuwar mahaifiyata?." kallon cikin eyes ɗinsa take ta maida masa amsa da cewa "kamar yadda kaima kayi farin cikin kashe mun mahaifiyata ba..." Ba Junaid ba hatta malam lawan dake tsaye shima ya girgiza da jin kalaman Ayush, cikin ɓacin rai Malam Lawan yace "ke Ayshert wani irin magana kike yi haka ne?..." Ayush ta kalli Malam Lawan sannan tace "malam wannan Junaid shine wanda ya kashe mun mahaifiyata da tsohon cikinta, kuma bazan taɓa yafe maka ba, mungu azzalumin bawa..." Junaid idonsa ne sukayi jawur tsabar baƙin ciki ga duk ya fita hayyacinsa yace "Yushert a lokacin da nake tambayarki shin wacece ke, kasa bani amsa kika yi, shin meyasa kika ɓoye mun kanki? duk da baki gaya mun ba naji kuma an sanar mun ko ke wacece a guri na, ko ba komai nasan tushen mahaifina kuma na gano su waye ƴan uwana, Yushert ko ba soyayya zanyi alfahari dake a matsayin ƴar uwata kuma jinina, mahaifiyarki kuma bani na kasheta ba, ta ceci rayuwata ne...." Kafin ya ƙarasa maganar Ayush ta kai hannu ta zabga masa mari asaman fuskarsa, Lailah ce tayi wani irin firgita tasa hannu biyu ta toshe bakinta tana zaro ido waje, Shima Doctor Hasheem dake bakin ƙofar ɗakinsa a tsaye saida ƙirjinsa ya buga, Malam ne yayo kan Ayush yana faɗin "kin haukace ne Ayshert, shin kinada hankali kuwa?..." Junaid haka yake bin Ayush da kallo cike da mamaki ya kasa aikata komai, tana kuka tace "Ni ba abunda zaka gaya mun Junaid, ka riƙe ɗan uwantakar ka domin ni yanzu babu wata alaƙa dake tsakanin mu, na tsaneka wallahi bana ƙaunar ganin fuskarka, ka kashe mun mahaifiyata sannan kazo kana mun wani banzan shirmen maganarka, zan gaya maka gaskiyar magana shine kamar yanda ka hallaka mun mahaifiyata toh haka nima na dasa gobara a cikin gidanku munyi two zero kenam, nima saidai ka kashe ni..." tana ƙarasa maganar ta rufa da gudun gaske ta shige ɗakin da take tasa sakata... Junaid jin furucin Ayush yasa yayi baya zai faɗi yana dafe da goshinsa Malam Lawan yayi saurin riƙoshi ya rungume shi sosai a jikinsa, haka jikin Junaid yake ɓari yana kakkarwa sosai ga duk gumi ya wanke masa ilahirin jikinsa, haka ƙirjinsa yake ta faman bugawa da ƙarfin gaske, Malam Lawan shima kamar a mafarki yake jin kalaman Ayush domin yayi matuƙar tsorata sosai da abunda Ayush ta aikata kuma bata ji fargaban faɗa ba... wani irin ihu Junaid ya rausa ya durƙusa ƙasi da gwiwowinsa yana dukan ƙasa da hannayensa biyu da ƙarfin gaske, yana ihu kamar ransa zai fita.. haka Malam Lawan yake rungume dashi a ƙasi yana rarrashinsa, kamar zaiyi kuka haka yake ji, Doctor Hasheem shima yana tsaye yayi matuƙar tausayawa Junaid, Lokaci guda kuwa yaji Ayush ta fita masa arai kwata-kwata, a wannan lokacin ba ƙaramin haushi ta bashi ba, Lailah itama fashewa tayi da kuka ta nufi ɗakinta da gudu, tana zuwa ta zauna a bakin gado tayi dialing call number wata mutumiyarta ƴar jarida, bugu ɗaya kuwa ta ɗauki ƙiran, Da sauri Lailah ta kara a kunne tana faɗin "Hello Sumaiya kina inane?..." A ɓangaren Sumaiya kuwa cewa tayi "ina wajen aiki mana.." Lailah tace "toh kar ki bar wajen gani nan zuwa akwai tattaunawar da zamuyi, kuma hanyar samun kuɗin ki.." Sumaiya tace "Allah yasa rahotanni zaki kawo mun tsararru.." Lailah tace "maganar akan Doctor Fateema ne, gobarar da ya tashi da ita ba haka kawai bane, yarinyar gidan ce ta ƙoneta, yanzu haka tana gidan mu.." Sumaiya tace "amma kuma ance yarinyar itama ta ƙone a cikin gidan?..." Lailah ta kuma cewa "duk shiri ne, yanzu haka tana ɓoye a gidan mu, a tunanin mutane sun ɗauka ta mutu.." Sumaiya ta kuma cewa "Amma Lailah fatan dai kinada hujjoji a hannunki saboda bama aiki sai mun tabbatar da gaskiyar lamarin..." Lailah tace "ni ce kuwa mai tattare da hujjoji, domin har recording ɗin maganar ta cewa ita ta ƙone gidan inada shi, sannan inada photonta da video duk maganganun da takeyi, inaso ku buga jaridu akanta sannan ku bubbuɗe duk wata kafar television ku tallata ta da duk wasu maganganun da tayi, inaso hukuma tayi aiki akanta, abi hakkin Doctor Fateema..." Sumaiya itama ta gamsu da bayanan Lailah tace "shikenam zan sanarwa Ogan mu kuma zaiyi farin ciki sosai dajin wannan batun domin ba ƙaramin kuɗi zamu samu a kafar mu ba, mungode sosai Lailah, yanzu kizo ki bamu duk wasu bayanai, inba sa'a ba sai anyi zanga-zanga akan a hukunta yarinyar..." Lailah murmushi tayi sannan tace "shikenam saikin ganni..." daga nan sukayi sallama.. Daƙer Malam Lawan ya rarrashi Junaid suka tashi har saida Doctor Hasheem yasa hannu suka fita da Junaid, domin kasa tafiya yayi ƙafarsa ta riƙe, ga zazzaɓin da yake kawo masa hari... Ayushert tana daga cikin ɗakin tana jin ihun da Junaid yake yi gaba ɗaya ji takeyi kamar ta kashe kanta, itama kukan take sosai, tana cikin kukan sai taji murɗa yana damunta da sauri tasa hannu ta toshe bakinta tana yunƙurin amai! tashi tayi da gudun gaske ta nufi toilet, haka take kwarara amai kamar ranta zai fita, duk abunda taci saida ta amar dashi, har ta koma tana aman zallar ruwa... haɗagowa tayi tana maida numfashi sama-sama, domin ba ƙaramin wahala take sha ba, lokaci guda ta fita hayyacinta... Narasimha tin tinin yazo ya ɗauke Damusa sun ɓace tare..... *TOFAH KAR DAI ACE YUSHERT CIKI GARETA🤔🤔🤔* *TAFIYAR OGAH JUNAID DA DAWOWARSA ONE MONTH...* *TAYI 3 MONTHS A GIDAN DOCTOR HASHEEM...* *4MONTHS KENAM🙄🤔🤔 NIDAI NA FARA LISSAFI..* 𝑡𝑦𝑝𝑖𝑛𝑔✍️ 𝗠𝗔𝗧𝗔𝗥 𝗗𝗔𝗠𝗨𝗦𝗔 the wife of a tiger🐅🐅🐅🐅 𝙼𝚊𝚕𝚕𝚊𝚔𝚒𝚗 𝙰𝚜𝚖𝚎𝚎𝚝𝚊𝚑 ✍️✍️ 𝙿𝚊𝚒𝚍 𝚋𝚘𝚘𝚔 𝚌𝚊𝚕𝚕 𝚘𝚛 𝚠𝚑𝚊𝚝𝚜𝙰𝚙𝚙 09065443871 *💫💫{{N W A}}💫💫* Book two C̶h̶a̶p̶t̶e̶r̶ 41 ➡️ 42 Bayan Malam Lawan sun isa gida daƙer ya rarrashi Junaid, duk da har yanzu jikin nashin ba ƙwari, Junaid yana jan ƙafa ya shige ɗakin da yake a gidan Malam Lawan, yana shiga ya tarar da Damusa baya nan ƙirjinsa ne yayi wani irin bugawa daiden lokacin shima Malam Lawan ya shugo, da sauri Junaid ya waiwayo yana faɗin "ina Sujjur?.." Malam Lawan yayi murmushi yace "kwantar da hankalinka Sujjur ya tafi yana can cikin ƙoshin lafiya" Junaid cike da mamaki yake kallon Malam Lawan yace "bangane ba, shin ina ya tafi?.." yace "Junaid kenam ai masu masarauta bazasu bar Sujjur ya zauna a gefe guda ba, an bi ta hanyar tsafi an ɗauke shi..." Junaid yace "toh amma waye yazo ya ɗauke shi?.." Malam Lawan yace "Narasimha babban matsafine a cikin masarautar shine mai basu kariya akoda yaushe..." Jinjina kai Junaid yayi sannan yace "ok na sanshi..." ya ƙarasa maganar tareda zama a bakin gado yana dafe da kansa, maganganun Ayush ne suka fara masa yawo a ƙwaƙwalwa, lokaci guda kuwa saiga hawaye yanda yake ta gangaro masa, cikin sassanyar murya yace "why! why!! meyasa Yushert zata mun haka, mahaifiyata ta ƙona da wuta, saboda wani ƙudirinta da ban, meyasa zatayi wa mommy haka bayan tayi mata halacci a rayuwa..." ya ɗago yana kallon Malam Lawan wanda shima tagumin yayi yana jinjina maganganun Ayush, Yace "tabbas ba ƙaramin kuskure ta aikata ba, ban taɓa tunanin zatayi haka ba.." Junaid dafe goshinsa yayi yana zubda hawaye, ji yayi malam lawan ya dafa kafaɗarsa yana rarrashinsa tareda faɗin "kayi haƙuri Junaid, kar ka biyewa zuciyarka ka aikata wani mummunan abu, inaso ka jirani ina zuwa yanzu..." yana kaiwa nan ya miƙe ya fice... Bayan minti goma sai gashi da ƙaton littafi a hannunsa da wani ɗan ƙaramin akwati, Junaid ɗagowa yayi yana kallon Malam Lawan, yace "wannan littafin da na kawo maka kwanaki ne ai.." Malam Lawan yace "ehh yanzu zan karanta maka tarihin rayuwar iyayenka da kakanunka sannan saika ɗauko mun ɗayan littafin da Narasimha ya baka, anan zaka gama fahimtar ko kai waye ne..." Junaid shidai kawai kallon Malam Lawan yake da lufu-lufun idanuwansa waɗanda suka canza sukayi jawur... Malam Lawan ne ya fara kora masa labari tin daga farkon haihuwar mahaifinsa har zuwansa Nigeria, Malam Lawan kaf saida ya bayyana komai, da kuma silar kamuwa da ciwon Damusa har warkewarsa sannan ya bayyanar masa akan cewa Ayush ce tayi silar warkewarsa ta hanyar cire wannan zoben jikin cibiyarta... Bayan Malam Lawan ya gama da littafi na ɗaya haka yasa Junaid ya ɗauko masa littafi na biyu nan ma ya fara bayyana masa labarai na tarihin rayuwarsa dana Ayushert, Kamar yadda Narasimha ya bawa mommy labarin masarauta haka malam Lawan shima ya bada wa Junaid labarin kaf ba abunda ya bari,. ya gama bashi labarin daiden lokacin anata ƙiraye-ƙirayen sallar mangarib, Junaid ba ƙaramin jijjiga yayi ba a wannan labarin gaba ɗaya ya shiga taitayinsa, fuskar nan ta koɗe har wani yellow+² yayi tsabar firgicin da ya shiga da tashin hankali, idonsa kamar wanda yayi shaye-shaye daƙer yake lumshe su ga fatar lips ɗinsa duk ya bushe, kana ganin Junaid kasan ba ƙaramin jiki yake sha ba, duk ya fice a kamannunsa ya rarrame lokaci guda, wani irin ƙaunar Ayush ne yaji ta shige masa zuciya domin ba ko wace mace bace zata ita sadaukar da rayuwarta akan wani ba, kuma ta dajirce sosai akan Junaid, ta ɗauki duk wani wahalarsa, ta kuma jure duk wulaƙancin da yayi mata... Jinjina kai yayi a hankali ya furta "tabbas soyayyar gaskiya bazata taɓa gushewa ba, bazan taɓa rabuwa da Yushert ba domin bazan samu mace kamarta ba, Mommy tamkar mahaifiya take a gurin Yushert don haka nabarwa komai a hannun Allah, shine mai yanda yaso nidai burina Yushert ta dawo gareni, inaso na biyata da nawa dubun alkhairin data aikata mun a baya, zan sa a raina cewar mu marayu ne daga ni har ita wanda ya rage mana mutum ɗaya ne shine mahaifinta kuma mahaifina wato sarki Raamud..." Junaid ya ƙarasa maganganunsa tareda miƙewa tsaye... Malam Lawan yace "toh daka miƙe tsaye ina zakaje?.." Junaid kallon Malam Lawan yayi sannan yace "zan koma gurin Yushert, zanje na tafo da ita domin ita ɗin rayuwata ce kuma jinin jikina..." Malam Lawan yace "idan kaje Ayshert bazata taɓa sauraronka ba a halin yanzu, zata walaƙantaka ne.." Junaid yace "zan iya juran duk wani wulaƙancin ta Malam, nidai burina ta kasance dani..." Malam Lawan ne ya riƙo hannunsa yace "shikenam! Shikenam!! yanzu dai zauna inaso na baka wani albishir ɗin labari wanda yau zakayi ƙwanan farin ciki" Junaid jin wannan batun yasa ya zauna cikin gaggawa yana facing ɗin Malam, gaba ɗaya yana ɗaukin malam ya sanar masa, gani yayi malam yasa hannu ya ɗauki wani ɗan ƙaramin akwati wanda yayi baƙi ƙirin daka ganshi kasan acikin wuta aka ciro shi, Junaid yana kallon akwatin yace "wannan kamar boxes ɗin mommy.." Malam Lawan yana jinjina kai yace "shin kasan meye a cikinsa?.." Junaid ya jijjiga kai alamar a'ah, malam Lawan yana murmushi yace "wannan ɗan ƙaramin akwatin a cikin shirgin mommy na ganshi, komai ya ƙone amma banda shi sakamakon jikinsa na ƙarfe ne..." yasa hannu ya buɗe cikinsa ya ɗauki card guda ɗaya ya miƙawa Junaid, da sauri ya karɓa yana dubawa, ƙirjin Junaid ne yayi wani irin bugawa da ƙarfin gaske ganin a jikin katin an manna photonsa dana Ayush kuma ga sunansu a jiki.. Junaid miƙewa yayi da sauri yana faɗin "Malam wannan kamar katin Aure koh?.." Malam yana murmushi yace "ba alamar tambaya Junaid! hakane ka duba date ɗin da aka ɗaura muku Aure kai da Ayushert, a washe garin zaka tafi yaƙi aka ɗaura Auren, kuma a ranar da Angela ta musulunta a ranar aka ɗaura Auren ba tareda kun saniba, ban san dalilin da yasa mahaifiyarka ta ɓoye muku ba, amma mune shaidun Aurenku domin nine maɗaurin Auren Ayshert kai kuma Barrister Aminu ne abokin mahaifinka..." Junaid kamar zai sume a gurin tsabar farin ciki haka ya ɗora katin a saitin zuciyarsa yana fitar da numfashi a hankali ga wani irin murmushi a saman fuskarsa har saida dimple ɗinsa suka lotse yace "Allah na gode maka, Allah Ubangiji ya sakawa mahaifiyata da gidan Aljanna, ina Alfahari dake mahaifiyata, taga zuciyata ina ƙaunar Yushert sosai..." Malam Lawan yace "Ma sha Allah, yanzu dai taho muje muyi sallah saika ci abinci cikin nutsuwa tinda farin ciki ya wanzu maka..." Junaid yace "Malam idan nayi sallah zanje na ɗauko matata.." Malam yace "a'ah ka bari sai gobe da safe sai kaje ka fahimtar da ita, idan ta yadda kun tafo shikenam, idan kuma bata yadda ba saika barta dani ni zanje na ɗauko maka ita cikin fahimtar juna..." Junaid jinjina kai yayi da smile a kan fuskarsa yace "shikenam malam Allah ya kaimu goben.." Amma ba haka yaso ba, lokaci guda kuma sai yake jin wani irin ƙololuwar baƙin ciki sakamakon zamanta a gidan Doctor Hasheem kuma tana mazannin matar Aure, sai kuma ya fara jin kishi a ransa... ****** Lailah tana tare da Sumaiya ƴar jarida duk ta gama basu wasu bayanai da hujjojin da zasu bayyana Ayush a matsayin mai laifi, Sumaiya ce ta kalli Lailah tace "gaskiya kinyi ƙoƙari mutumiyata, kin bamu duk wasu bayanai da ake buƙata insha Allahu zuwa nan da kwana uku zaki fara ganin photunan Ayushert da video maganganun ta a gidan television, toh amma saidai Yayanki Hasheem shima zai fito a cikin jaridar mu saboda shine ya ɓoyeta kuma zamuje har ƙofar gidanku tareda tarin ƴan jaridu da masu ɗaukan rahotanni, kuma nasan tabbas dole ƴan sanda da sojoji zasu je domin kamota because mahaifiyar Captain Junaid ta kashe..." Lailah murmushi tayi tace "saina jiyo ku ƴar uwa..." tana kaiwa nan tayi tafiyarta... Lailah bata koma gida ba sai waran ƙarfe 10 na dare saboda ta wuce gidansu Maimoon domin jin wasu matsalolinta, ta shiga damuwa sosai ganin halin da Maimoon take ciki ga kuma cikinta ya fito sosai, tana kuma tausayawa Yayanta idan maganar nan ta fito... shugowa cikin falo tayi ta tarar da Ayush zaune a one seater tana kallon tv sai kuma Doctor Hasheem a 3 seater, zuwa tayi zata wuce ɗakinta da sauri Doctor Hasheem ya katse mata hanzari tareda faɗin "baki iya sallama ba koh?.." tsayawa Lailah tayi ba tareda ta juyo ba tace "nayi mana sai dai baku jini ba.." tana wani kumbura domin ta tsani ta tashi taga Ayush a cikin gidan nan, gaba ɗaya bata da wargi.. Doctor Hasheem ya kuma cewa "ina kika je?.." Lailah tana turo baki tace "gidansu Maimoon" ƙirjin Doctor Hasheem ne ya buga an fame masa ciwon dake zuciyarsa, cije leɓɓen bakinsa yayi yana jinjina kai tareda kallon Ayush wacce idonta akan tv, yace "Okay kije kitchen ki haɗowa Ayushert tea mai kauri ki kawo mata tana jin yunwa..." Juyowa Lailah tayi tana faɗin "Yaya kafin nabar gidan nan fah nayi girki, ai bai kamata ace abincin har ya ƙare ba saboda nasan ba baƙi akayi ba.." Doctor Hasheem yace "ehh ta cinye yanzu kuma tana buƙatar ruwan tea kafin ta kwanta idan kuma bazaki yi ba, Ni zan shiga kitchen na haɗo mata.." Lailah kamar zata rausa ihu tana jumping da ƙafafuwanta tana gunaguni tace "wannan matar akwai shegen ci kamar mayya, tinda tazo gidan nan girki sau biyu zuwa uku nakeyi tsabar cinta yayi yawa, munafuka kawai..." haka ta nufi kitchen tana wannan maganganun ba tareda Doctor Hasheem ya jiyota ba, amma saidai Ayush duk taji abunda ta ce, Doctor Hasheem jin gunagunin da takeyi ne yasa shi faɗin "Lailah kina magana ne?.." tace "a'ahh..." Bayan minti talatin saiga Lailah ta fito hannunta ɗauke da cup na ruwan shayi da haɗin madara, tana zuwa gaban Ayush ta miƙa mata, a cikin zuciyarta kuwa cewa tayi "ƴar buro uba na watsa miki dai akan fuska, acici mala'ikun tauna.." Ayush tana murmushi tasa hannu ta karɓa tareda cewa "yauwa ƴar ƙanwata godiya nake.." Lailah wani irin harara ta watsa mata ba tareda ta ganta ba sannan tayi wucewar ta ɗakinta tana kumbura kamar filfila,.. ****** Around 11:00pm Junaid yana ƙwance a saman gadonsa yana kallon ceilling sai murmushin yake shi kaɗai ga kuma katin Auren su a saman ƙirjinsa, fuskan Ayush ce take masa gizo, sai kuma yake tunowa da abunda ya faru a tsakanin su kafin ya tafi yaƙi, lokaci guda kuma ya tuno da Mommynsa saiga wani irin zazzafan hawaye yana faman gangaro masa, yana cikin wannan tunani-tunanin har bacci yayi awon gaba da shi... _________________Lailah ce ta tashi cikin dare ta fito falo sanye da sleeping dress riga da wando ta nufi frig ta ɗauki lemon juice kai tsaye ɗakin Doctor Hasheem ta nufa tana zuwa ta fara knocking a hankali har sai da tayi sau uku tukun yayi magana tareda faɗin "waye?.." Lailah tace "Ni ce dai Yaya.." bai sake yin wata magana ba sai ji tayi ya buɗe mata ƙofa ya juya ciki, itama bin bayansa tayi ta samu ɗaya daga cikin kujerun ɗakin ta zauna tana shan lemonta, Doctor Hasheem kallon agogon ɗakin yayi yaga kusan ƙarfe 12 na dare yace "meyasa kika tashi a cikin wannan daren?.." Lailah tace "daman ai ina tashi shan lemo ko cin Apple saboda yunwan dare ke damuna.." kallonta Doctor Hasheem yake cikin takaici yace "kuma sai akace kizo ki takura mun a wannan daren?..." turo baki Lailah tayi sannan tace "haba Yaya amma dai kasan bana zuwa maka a cikin dare ko? yanzun ma matsala ce ta kawo ni..." yace "matsalar bazaki bari saida safe ba?.." tace "yoo Yaya da safe ka tafi gurin aiki kodan yanzu an bada hutun asibitin koh? sakamakon mutuwar mai asibitin da aka kasheta, yanzu kullum kana tareda da wancan yarinyar taya zan samu lokacin zama dakai har mu tattauna akan matsalar...". ta ƙarasa maganar tana murguɗa baki tareda zuƙan lemonta, Doctor Hasheem kallonta kawai yake yana mamakin iyeyi da kinibibi irin na Lailah ga kuma bakin mayar da magana tana yarinya ƙarama, wanda yanzu take shirin shiga 19years old, girgiza kai kawai yayi yace "Allah ya shiryeki Lailah, yanzu dai meye matsalar daya kawo ki bacci nake ji..." tana kora ƴar lemonta hankali kwance tace "Daman maganar shine akan Maimoon tana da tumbi.." Doctor Hasheem cikin rashin fahimta yace "bangane Maimoon tanada tumbi ba, kowa ma ai yanada tumbi..." Lailah tana lumshe ido tace "ehh amma ai ba kamar namu ba, ita nata na musamman ne..." Doctor Hasheem yace "kinga bana son shirme fah idan bazaki gaya mun magana ba ki tashi ki tafi.." miƙewa tayi tana faɗin "a'ah Yaya ba saika koreni ba, zan gaya maka yauwa, daman Maimoon tanada tsohon cikinka..." zaro ido waje Doctor yayi yace "ban fahimta ba.." Lailah juyawa tayi zata fita tareda cewa "toh shikenam Yaya karka fahimta randa ta haihu kam ai zaka fahimta koh, idan nan ma baka fahimta ba saika jira isowar motar police a cikin gidan nan zakafi fahimta da kyau..." kafin Doctor Hasheem ya ce wani abu har ta fice da sauri ta nufi ɗakinta, Doctor Hasheem yana tsaye idonsa a bakin ƙofa tin lokacin fitar Lailah yanata maimaita maganar Lailah akan Maimoon tanada tsohon ciki, nan danan kuma gumi ya fara tsirto masa yana furta "ciki! ciki kuma? Maimoon daman akwai ciki? Innalillahi wa inna ilaihi raju'un..." A wannan lokacin kwana yayi bai rintsa ba, yanata tunanin Maimoon.... Itama Ayush tana can ɗakinta tana zaune ta kasa yin bacci, daga ta ƙwanta sai taji murɗa, gaba ɗaya ta fita hayyacinta tsabar yawan Amai, kuma komai taci saita amar tana cin abinci zata amar dashi hatta ruwa idan tasha baya zama mata a ciki, shiyasa take yawan jin yunwa har Lailah tana mata gorin yawan cin abinci, Yunwa ne ya gama isarta haka ta tashi ta fito falo kai tsaye kitchen ta nufa taje ta haɗo kakkauran shayi da biredi ta fito ta koma ɗakinta, zama tayi a bakin gado tana cin bread ɗinta da shayi ko rabin ci batayi ba wani irin murɗa ya hautsino mata, da gudun gaske ta nufi toilet bayan ta ajiye kayan bread akan mirror, amai takeyi bana wasa ba, kamar zata amar da kayan cikinta haka take ƙwaƙulo amai, Idanuwanta ne sukayi zuru-zuru ga wani irin hajijiyan da yake ɗibanta, fashewa tayi da wani irin matsanancin kuka tana faɗin "wannan wani irin masifa ne da bala'i, wai kam meyake damuna haka ne, duk abunda naci saina amar dashi, toh kenam haka zanyi rayuwata ba tareda naci komai ba, wayyo Allah nashiga uku..." haka take magana cikin kuka duk ta rarrame ta kokkoɗe ta gama tuttujewa, haka ta wanke bakinta tana tafiya tana laluman jikin bango tsabar hajijiyan da take ji, daƙer ta shiga bedroom ta faɗa akan gado rubda ciki tana kuka, ai kuwa saiga wani aman ya tunkaro maƙogaronta, wani irin hautsinawa tayi daga saman gadon ta faɗo ƙasi tana rarrafe ta shige toilet, a wannan lokacin kam a ƙasin tiles tayi aman domin bazata iya miƙewa tsaye ba, cikin natan nan kamar wanda aka yashe komai, tsabar yunwar da take ji, ga tumbin cikinta har ya ɗan soma fitowa amma duk bata gane cewar ciki bane gashi har na tsawon 4months, zama tayi a cikin toilet daga taji amai saita kwara shi a wajen, da haka har bacci ya ɗauketa a zaunen ta jingina bayanta a jikin bango, kayinta a sama da haka take baccin, cikin ya hanata cin abinci sannan ya hanata ƙwanciya, daga tayi ne sai Amai koda bazata amar da komai ba haka zata rinƙa kakakin Amai, tana zaune a toilet tana bacci jikinta har wani kakkarwa yake ga wani zazzaɓin da yake damunta, jikinta duk ya ɗau zafi, har wani canza colour tayi tsabar azaba launinta ya koma yellow...... *TOH PAH 🤣🤣🤣 ALLAH SARKI AYUSH HAR KIN BAN TAUSAYI WOLLAH...* 𝑡𝑦𝑝𝑖𝑛𝑔✍️ 𝗠𝗔𝗧𝗔𝗥 𝗗𝗔𝗠𝗨𝗦𝗔 the wife of a tiger🐅🐅🐅🐅 𝙼𝚊𝚕𝚕𝚊𝚔𝚒𝚗 𝙰𝚜𝚖𝚎𝚎𝚝𝚊𝚑 ✍️✍️ 𝙿𝚊𝚒𝚍 𝚋𝚘𝚘𝚔 𝚌𝚊𝚕𝚕 𝚘𝚛 𝚠𝚑𝚊𝚝𝚜𝙰𝚙𝚙 09065443871 *💫💫{{N W A}}💫💫* Book two C̶h̶a̶p̶t̶e̶r̶ 43 ➡️ 44 Bayan sallar Asuba da sassafe sai ga motar Junaid a ƙofar gidan Doctor Hasheem, buɗe murfin motar yayi ya fito da hanzarinsa hannunsa riƙe da katunan Aurensu, buga gate yake da ƙarfin gaske,. daga ciki ne maigadi yace "waye ne fisabilillahi da sassafen Allah" ya ƙarasa maganar yana buɗe gate ɗin! ganin Junaid ne yasa shi washe baki yana faɗin "ahoo ashe yallaɓai ne, sannu da zuwa" bai ƙarasa maganar ba Junaid ya bangaje shi tareda shige wa ciki, da gudun gaske ya ƙarasa zuwa cikin gidan yana zuwa nan ma ya fara buga musu ƙofar falo, har saida ya buga kusan sau biyar kafin yaji motsin mutum, Doctor Hasheem ne ya buɗe yana yamutsa fuska yace "lafiya kuwa Junaid da sassafe kazo gidan mutane?.." Junaid ne yake masa kallon up and down sannan yace "ina matata?.." Doctor Hasheem cike da mamaki ya maimaita cewa "matarka kuma? aina kenam?.." Junaid ne ya zuciyo ya cabki ƙwalar rigar baccin Dr Hasheem yana faɗin "nace ina matata Yushert? kayi kuskuren zama mun da mata a cikin gida ɗaya Doctor Hasheem, Yushert she's my wife don haka ka bani waje naje na ɗauko matata.." Doctor Hasheem jin abunda Junaid yake faɗi ne yasa shi kwashewa da dariya yana nuna shi da yatsa, dariya kuwa yaƙi tsayuwa har wani kama ciki yake, daƙer ya tsagaita dariyar yana faɗin "shin ka haukace ne Junaid? taya Ayushert ta zamo matarka? kodai a daren jiya kayi mafarki ne toh kuwa idan mafarki kake gwara ka farka domin a halin yanzu Ayush tafi ƙarfinka, yanda ta tsaneka a rayuwa ai kana sanar mata cewa ita matarka ce zuciyarta bugawa zatayi..." ya ƙarasa maganar yana dariya yatsarsa akan Junaid yana nuna shi.. A fusace Junaid ya kama yatsar yayi baya da ita sai ƙarasss ya karya ta, wani irin ihu Dr Hasheem yayi saida ya tayar da su Lailah da Ayush, maigadi kuwa da gudu ya nufo gurin yana zazzaro ido waje, Doctor Hasheem wani irin mahaukacin naushi yakai wa Junaid da sauri Junaid ya damƙe hannun da hannunsa ɗaya sannan yayi wurgi dashi gefe, Miƙewa Doctor Hasheem ya kuma yi yana ihu yayo kan Junaid kafin ya ƙariso Junaid ya girbe masa ƙafa har saida yayi sama tukun ya doku a ƙasi daiden lokacin Lailah ta fito, itama ihu ta soma yi tana faɗin "dan Allah jama'a a kawo agaji za'a kashe mun Yayana wayyo Allah nahhhh.." Junaid zuwa yayi a gigice ya zabga mata wani irin mari har saida ta kife ƙasi yace "idan na sake jin ihunki saina cire miki haƙwarai.." Ɗagowa Lailah tayi tana toshe bakinta da hannu bibbiyu tana girgiza masa kai, Doctor Hasheem ne yazo ta bayan Junaid ya ƙwaɗa masa wani ƙaton katako a gadon bayansa, kifewa yayi kamar zai faɗi ƙasi yayi saurin dafe ƙasa da hannunsa, ɗaga katakon Doctor Hasheem ya kuma yi zai ƙwaɗa masa a zabure Junaid ya juyo ya riƙe katako tareda girbe masa ƙafa ya kifu da bakinsa, shaƙe masa wuya Junaid yayi yana huci tareda faɗin "shin Yushert matarka ce ko matata?.." ta bayansa yaji Ayush ta amsa da cewar "Ni ɗin matarsa ce ba matarka ba.." Da sauri Junaid ya miƙe tsaye tareda waiwaya bayansa yana binta da kallo, bakinsa na motsi a hankali yace "Yushert..." kafin ya furta komai tayi saurin ɗaga masa hannu a tsawace tace "babu abunda zaka cemun Junaid, ka kyauta daka zo gidan mutane kayi musu duka, shin meya kawo ka?..." Junaid ne ya nufi gurinta tayi saurin dakatar dashi tana faɗin "dakata mun malam kada ka sake kazo yanda nake domin bana ƙaunar jin ƙamshin jikinka ma.." kawar da kanta gefe tayi tana kallon Doctor Hasheem wanda har zuwa yanzu yana ƙwance a ƙasi sai faman birgima yake tsabar ciwon da jikinsa yake masa, da sauri tayo kan Doctor Hasheem tana faɗin "sannu koh Doctor, kayi haƙuri Allah zai saka maka, indai mutum zalunci ya iya toh wallahi Allah bazai barshi ba, mutum ba imani a zuciyarsa ko kaɗan..." hannu tasa zata ɗago shi Junaid a fusace ya daka mata uban tsawa yace "kar ki taɓa shi Yushert..." ko ɗagowa ta kalleshi batayi ba haka tasa hannu tana ƙoƙarin ɗago shi Junaid yasa hannu ya finciko ta tareda zabga mata mari sauran kaɗan ta faɗi ƙasi yayi saurin tarota ya haɗeta da ƙirjinsa,. hannu tasa ta tureshi da ƙarfin gaske tana ja da baya tareda fashewa da kuka, Dr Hasheem tasowa yayi yana faɗin "meye dalilinka nasa hannu ka mareta? yanzu ni nake riƙe da ita ba kai ba..." Junaid a fusace yakai hannu zai naushe masa hanci Ayush tayi saurin shige wa tsakaninsu sauran kaɗan ya nausheta, tana kuka tace "wallahi wallahi wallahi Junaid ka sake dukan Dr Hasheem zaka daina gani na har abada domin ba abunda zai hana na kashe kaina kowa ma ya rasa, daman ai rayuwata kake bibiya ko? so kake kaga bayana to kuwa zaka gani..." Junaid cike da mamaki yake kallon Ayush yace "Yushert me kike faɗa ne haka?.." Ayush ce ta kalli Doctor Hasheem sannan tace "Doctor.." ya amsa cikin kulawa a yayin da idonsa yake kanta, tace "shin kana sona?.." ya amsa mata da cewar "sosai ma gimbiyar mata..". sauƙe numfashi tayi sannan tace "indai kana sona da gaske toh inaso a cikin wannan satin a ɗaura mana Aure.." Doctor Hasheem da ƙwarin gwiwarsa yace "an gama gimbiyata..." Junaid kamar ya rausa ihu yana nuna Ayush da disashshiyar murya yace "Yu Yu Yushertttt kefa matar Aure ce, Mommy ta rigada ta ɗaura mana Aure..." murmushi Ayush tayi sannan tace "My Doctor wannan ya haukace inaga saika koya masa hankali, ka ɗauki katakon nan kaita dukansa har saiya fita hayyacinsa, wannan umarni nane idan har kana sona da gaske..." tana kaiwa nan tayi juyawarta zata koma cikin ɗaki, Junaid kallonta yake ga hawaye yanda yake bin saman fuskarsa ya ware hannayensa biyu sannan ya durƙusa ƙasi da gwiwowinsa yana faɗin "Yushert tinda ke kika bada umarni ayi mun duka toh na amince, indai a kanki ne zan iya sadaukar da rayuwata, amma ki sani ina matuƙar ƙaunarki kuma keɗin matata ce jigon rayuwata, uwar ƴaƴana..." tsayawa tayi tana sauraronsa daga baya kuma ta shige cikin falo da gudu tana kuka... Duk abubuwan da akeyi Lailah tana zaune a ƙasi tana sauraronsu, Doctor Hasheem ne ya ɗauki katakon yana juyashi yace "dukan da kayi mun a wancan lokacin a asibiti ciwon yana nan bai warke ba, still yanzu ma ka maimaita, ai kuwa zan ɗau fansaaa..." ya ƙarasa maganar tareda jibga masa katakon nan ata bayansa, Junaid yana durƙushe a ƙasi yace "tinda Yushert ce ta baka umarni toh cigaba da dukana Doctor Hasheem...". haka Doctor Hasheem ya rinƙa kwaɗa masa katako ata ko ina a sassan jikinsa, har ya fasa masa kayi nan danan jini ya soma zuba, amma Junaid yana durƙushe ko motsawa baiyi ba, Lailah ganin Yayanta zaiyi wa Junaid illa a kayi yasa ta taso da gudu tana faɗin "Yaya dan Allah ka bari haka zaka kashe shi fa, Yayaaa..." ta riƙe Yayanta tana ƙoƙarin hanashi dukan Junaid, Doctor Hasheem cikin zafin rai ya hankaɗa Lailah gefe guda ta faɗi ƙasi goshinta ya bugu da floor da ƙarfin gaske, still ɗagowa tayi tana riƙe da goshinta tana faɗin "Yayaaa! Yayaaa!! ka ƙyale shi Yayaaa!!!..." cikin sassanyar murya take maganar ta gagara motsawa ko ina, kanta ne yake wani irin juyawa haka take kallon dishi-dishi tana lumshe ido tareda ƙara buɗe su a hankali, suffar wata mata take gani tana yowa kanta, tsugunawa tsohuwar matar tayi a gaban Lailah tana murmushi, zaro ido waje Lailah tayi tana kallon matar domin tana yawan zuwa mata a mafarki ta ƙarashi iskancinta da Lailah ta cikin mafarki, domin matar nan ne wacce ta haɗa Lailah da Maimoon lesbian, a yanzu Maimoon ta kuɓuce daga hannunta sakamakon cikin dake jikinta, ita kuma tsohuwar daga lokacin ta cire Maimoon a zuciyar Lailah, hakan yasa yanzu Lailah bata sha'awar Maimoon ko kaɗan sannan haka Maimoon yanzu ta samu lafiya, Sai kuma tsohuwar ta dawo da sha'awarta kan Lailah ita kaɗai, cikin dare take zuwa gurin Lailah ta gama maɗigonta ta ita, hakan yana matuƙar ɗaurewa Lailah kai saboda ita sai da safe tajita a jiƙe kuma jikinta a mace, tana kallon tsohuwar amma saidai babu halin dakatar da ita.. saboda haka Lailah bata lesbian da kowa saidai idan wannan tsohuwar ce tazo mata... Lailah tana zaune haka duniyar taketa juya mata a lokacin bata iya ganin kowa sai fuskar wannan tsohuwar, haka tsohuwar take ƙiran sunanta a sanyaye tana faɗin "Lailahhhh! Lailahhhh!! Lailahhhh!!! Ina sonki Lailahhhh, banaso ki shiga tashin hankali Lailahhhh, gashi yau kin saka kanki cikin firgici Lailahhh, zuciyarki bugawa take Lailahhh! Ƙwaƙwalwarki juyawa take Lailahhh!! Lailah kin rasa tunaninki, kin cutar dani, meyasa zaki rasa tunaninki alhalin inajin daɗin kasancewa tare dakeee, a yanzu kin zamo marar tunani, Yayanki yayi sanadiyar juyewar ƙwaƙwalwarki, ni kuma bazan iya kasance dake a haka baáaa, na barki Lailahhh, zan cire miki sha'awar maɗigo acikin ranki, daga yau bazaki ƙara yin maɗigo baa, daman maɗigon nawa ne kuma yanzu na karɓi kayataaa, kin rasa tunaninki kwata-kwata bazaki iya tuna abunda ya faru a baya baa sakamakon buguwar da kikayi, ƙwaƙwalwarki ƴar ƙarama ceee...." Haka tsohuwar nan ta ƙarasa maganganunta tana ambaton sunan Lailah, "Lailahhhh! Lailahhhh!! Lailahhhh!!! Lailahhhh!!!! na barki lafiyaaa...." daga nan tsohuwar ta ɓace ɓattttt... wani irin gigitaccen ihu Lailah tayi ta ƙanƙame kayinta sosai sakamakon juyawar da yake da sauri. itama faɗuwa tayi ta ƙwanta a ƙasi sumammiya... Ayush jin ihun Lailah ne yasa ta fito da gudu, ganin yanda Doctor Hasheem yake ta dukan Junaid ba ƙaƙƙautawa ga yanda jini yake ta zuba masa kuma yana durƙushe akan sawayensa, Da gudu Ayush ta rufo kan Junaid tana zuwa itama ta durƙusa ƙasi tareda rungumarsa tana kuka tana faɗin "dan Allah Doctor Hasheem ka barshi haka kar ka kashe mun shiiii..." ta fashe da matsanancin kuka, ta kuma rungumar Junaid sosai a jikinta, duk ta ɓata kayan jikinta da jinin Junaid... tana faɗin "hospital Dan Allah, kar ya mutu, ina buƙatarsa a raye Please a kaishi asibitiii.." Shima Junaid rungumar Ayush yayi yana kuka tareda faɗin "Yushert i love you! I love you my Yushert!! I love you my wife!!!..." Itama Ayush tana ƙanƙame dashi tana rera kuka mai taɓa zuciya... saitin kunnensa ta kawo bakinta tana rera masa waƙa... "you are my Sunshine🌞, my only sunshine 🥀🌞, you make me happy when skies are grey you'll never know 💫 dear how much I love you please don't take my sunshine🌞 away🥀🥀🥀🥀....." haka ta rinƙa raira masa waƙannan a cikin kunnensa tana rungume dashi, shi kuwa shuru yayi yana sauraronta ya ƙanƙameta sosai kamar wanda za'a raba su... Doctor Hasheem kai tsaye gurin da Lailah take a ƙwance ya nufa yana zuwa ya taɓa wuyanta yaji bata fitar da numfashi, yayi matuƙar tsorita sosai haka yasa hannu ya ɗauketa da sauri yaje ya buɗe murfin motarsa ya ƙwantar da ita a bayan motar shima ya zagaya ya shige, a ɗari ya finciki motar suka bar gidan daman maigadi ya buɗe masa gate ɗin, haka jikin maigadi yake rawa tsabar tsoro da firgici, yana tsaye sai haɗiyar yawu yake shi a tunaninsa har yanzu Junaid yana tiger ne, yana tsoro kar ya zama Damusa... Ayush tana cikin raira masa waƙa taji jikinsa yana kakkarwa sosai, ga yaɗau zafi over, kuma jininsa ya zuba sosai yana buƙatar temakon gaggawa, ƙara fashewa tayi da matsanancin kuka still bata daina waƙar ba, suna cikin wannan halin sai suka ji horn ɗin motar, maigadi ne yayi saurin buɗewa ba tareda ya duba ba, motar Malam Lawan ne ya shugo kai tsaye ko gama tsayar da motar baiyi ba ya fito da gudun gaske yayo kan Ayush yana faɗin "lafiya kuwa Ayshert meya faru da Junaid?..." Ayush ko ɗagowa ta kalli Malam Lawan batayi ba still tana kan rera waƙarta, kayinta a kwance saman kafaɗar Junaid wanda shima kansa a ƙwance yake saman kafaɗarta, shi kuwa tinin har ya suma numfashinsa ya ɗage cakk.. Daƙer Malam Lawan ya ɓanɓari Junaid daga jikin Ayush domin ba ƙaramin riƙo yayi mata ba duk da yana sume, Itama riƙe shi tayi sosai saida malam ya yageta a jikinsa tana kuka mai fitar hankali, Shi kuwa murfin motarsa ya buɗe ya saka Junaid a ciki shima ya shiga suka bar gidan.. Bayan fitarsu Ayush ƙwanciya tayi a ƙasin floor ta cigaba da rera waƙarta tana kuma kuka, idon nan yayi jawur ga fuska shima yayi jawur abunka da farar fata, Maigadi bayan ya rufe gate shima zama yayi akan kujerar robarsa yana fuskantar Ayush wacce take kwance a ƙasi kamar wacce take kan gadonta.... Malam Lawan kai tsaye hospital ya tafi da Junaid zuciyarsa cike da baƙin cikin abunda akayiwa Junaid... Shima Doctor Hasheem hospital ya kai Lailah amma saidai ba asibitin Doctor Fateema yakai ta ba, wani asibiti daban yakaita.... ******* Maimoon tana durƙushe a gaban Daddynta a falo shi kuwa yana zaune akan kujera yana fuskarta ta ga wuƙa a hannunsa yace "Bintu zaki gaya mun wanda ya miki ciki ne ko saina yanka ki yanzun nan?..." tana kuka tace "Daddy wallahi ban saniba, mutanen da suka sace ni ne suka mu kuma ban san su baa.." Daddy cije leɓɓensa yayi cikin takaici yake faɗin "Bintu a baya na yarda dake sakamakon kinada hankali ga kuma biyayyar da kike mana, banida ko wace ƴa inba ke ba, ke kaɗai Allah ya mallaka mu! na ɗauki son duniya na ɗora miki, Allah ya baki ilimin boko da Arabic, a fannin boko kin gama degree ɗinki, a fannin Arabic ke malamar islamiyya ce kin haddace alƙur'ani mai girma, amma wai yau ani zaki bawa kunya a idon al'umma? haba Bintu! toh wallahi wallahi bazan taɓa yadda dake ba shin waya miki ciki?..." Maimoon fashewa tayi da matsanancin kuka ga ciki ɗurumma agaba tace "Daddy gaskiya na faɗa maka..." cikin takaici Daddy ya kamo hannun Maimoon ya yanka da wuƙa, nan danan saiga jini kamar ambaliya, haka take ihu kamar ranta zai fita... Cikin tsawa yake faɗin "zaki gaya mun wanda ya miki ciki ko saina yanke hannun gaba ɗaya? kar ki manta fahh an taɓa gaya mun cewa an ganku a hotel ke da Lailah shin me kuka je yi? gurin wa kuka je a hotel? an gaya miki ni sakaran uba ne wanda zan zuba miki ido kiyi abunda kike so?..." Ammy tana can ɗakinta tana ƙwance in banda kuka ba abunda take, bazata iya juran ganin hukuncin da ake yiwa Maimoon ba... Daddy haka ya kama hannun Maimoon ya rinƙa yankewa tin daga kan dantsenta har zuwa tafin hannunta haka yake sa mata wuƙa yana yankewa, kamo ɗayan hannunta yayi shima ya rinƙa dasa mata wuƙa, nan danan jini kamar ambaliya duk ya wanke mata jiki da wajen da take zaune, a cikin tana ihu har ta komo hankalinta ya soma fita daga jikinta, haka take lumshe ido kamar zata mutu, Daddy magana yake mata amma ta kasa yin magana, Haka ya tashi a fusace ya nufi ɗakinsa kafin ya dawo Maimoon har ta ƙwanta hankali yana shirin fita, can saiga shi ya dawo hannunsa riƙe da Allura ganinta a ƙwance ya darara mata uban tsawa yana faɗin "waya baki izinin ƙwanciya dan ubanki, tinda har ni zaki tozarta toh zanyi maganinki, bazan taɓa jin tausayinki ba tinda har kema bakiji tausayin kanki ba, yau ko kinaso ko bakya so saikin gayi wanda ya miki ciki! bazan barki ba saidai idan mutuwa kika yi a yanzun nan..." ya ƙarasa maganar yana caka mata allura a dantsenta, wannan allurar bana komai bane sai fitar da mutum daga hayyaci yasa ya faɗi duk wata gaskiyar da aka tambaye shi... Bayan wasu sakonni Maimoon tana ƙwance ta kasa tashi zaune ga yanda idonta yake juyawa, bakinta yana kakkarwa kamar mai jin sanyi, haka haƙwaranta suke dukan juna tsabar kakkarwar da suke yi.. Gyara zama Daddy yayi yana kallon Maimoon yasan a wannan lokacin Alluran ya gama bin jikinta yace "Bintu gaya mun waye ya miki ciki?..." Maimoon baki na kakkarwa tace "D D Doc Doct Doctor Haa Haas Haashim neee, ya yaa yamuun f f fya fyaɗee...." Daddy daƙer ya fahimci abunda Maimoon ta gaya, Ƙirjinsa ne yayi wani irin bugawa da ƙarfin gaske ya miƙe tsaye tareda faɗin "Whatttt! Doctor Hasheem?..." *Toooh Matan Tigers kuna Ina neee* *Nidai bakina da goro babu abunda zancen* 𝑡𝑦𝑝𝑖𝑛𝑔✍️ 𝗠𝗔𝗧𝗔𝗥 𝗗𝗔𝗠𝗨𝗦𝗔 the wife of a tiger🐅🐅🐅🐅 𝙼𝚊𝚕𝚕𝚊𝚔𝚒𝚗 𝙰𝚜𝚖𝚎𝚎𝚝𝚊𝚑 ✍️✍️ 𝙿𝚊𝚒𝚍 𝚋𝚘𝚘𝚔 𝚌𝚊𝚕𝚕 𝚘𝚛 𝚠𝚑𝚊𝚝𝚜𝙰𝚙𝚙 09065443871 *💫💫{{N W A}}💫💫* Book two C̶h̶a̶p̶t̶e̶r̶ 45 ➡️ 46 Lailah tana ƙwance saman gadon asibiti an saka mata na'urar auna ƙwaƙwalwa a kanta, sai tarin likitocin da suke dubata waran su uku, Shi kuwa Doctor Hasheem yana zaune akan ɗaya daga cikin kujerun asibiti yana jiran fitowar likitocin, yayi tagumi yanata tunanin abubuwan da suka wakana, lokaci guda kuwa ya fara girgiza kansa yana faɗin "Please Ogah Junaid am so sorry, nayi regretted abunda na aikata maka, dan Allah ka yafe mun..." yana cikin wannan maganar zuci yaji an dafa kafaɗarsa ta baya da sauri ya waiwaya tareda miƙewa tsaye yana faɗin "Doctor ya jikin ƙanwata fatan dai tana lafiya, shin ta farfaɗo ne?.." Girgiza kai Doctor yayi sannan yace "inason ganinka a office ɗina.." yana kaiwa nan Doctor yayi juyawarsa, gaban Doctor Hasheem ne yake yankewa duk jikinsa yayi sanyi da haka ya nufi office ɗin Doctor jiki ba ƙwari!..." yana zuwa kuwa ya samu Dr a zaune a cikin office ɗinsa shima Dr Hasheem guri ya samu ya zauna yana fuskantar likitan, gyaran murya Doctor yayi sannan yace "Ammm Dr Hasheem abunda zan gaya maka shine kayi haƙuri nasan zakaji ba daɗi amma inaso kayi la'akari da kaima Doctor ne kuma kuna samun irin waɗannan matsalolin a asibitinku, kamar yanda kuke cewa iyayen wasu suyi haƙuri toh nima yau zance maka kayi haƙuri ƙanwarka ta rasa tunaninta gaba ɗaya sakamakon buguwar da tayi akanta, ƙwaƙwalwarta ta juye bazata iya tuna duk abunda ya faru a baya ba, haka kuma bazata iya gane kowa a halin yanzu ba, ga sakamakon gwajin da mukayi mata..." Dr ya miƙawa Dr Hasheem wata doguwar takarda, jiki a sanyaye Dr Hasheem yakai hannunsa ya karɓi takardar hannu na kakkarwa, sannan ya buɗe yana karantawa lokaci guda saiga hawaye duk ya wanke masa fuska... Dr ne yake ta faman bashi haƙuri... Dr Hasheem yace "shin Dr babu wani maganin da za'ayi ta dawo hayyacinta?.." Dr Mansur yayi murmushi sannan yake "Hmmm Dr Hasheem kenam inda ace bakayi karatun Biosciences ba sai inyi maka uzuri amma kai fah kasan kan tsarinnan yanda yake, idan Allah yasa ta farfaɗo za'a ɗorata ne akan maganin sakatiri, kuma dole sai an kaita babban asibitin masu juyayyun ƙwaƙwalwa..." Dr Hasheem ne yace "shikenam Dr ni zan tafi, fatana Allah ya tashi kafaɗunta.." Dr Mansur yace "no insha Allahu zata tashi ma" ficewa yayi daga office yana sharar hawayen kan fuskarsa tareda duba agogon hannunsa misalin ƙarfe 10 ne na dare, shiga ɗakin da aka ƙwantar da Lailah yayi ya samu kujera ya zauna tareda kwantar da kansa a bakin gadon hannunsa riƙe dana Lailah sai faman zubda ƙwallah yake, Ita kuwa Lailah gaba ɗaya ta zama abun tausayi har zuwa yanzu bata farfaɗo ba, anyi recovery bakinta da hancinta da Oxygen, ga gefe da gefen kayinta na'ura ne a jone yana aiki da computer, hannunta kuma yana ɗaure da drip na ruwa... Can bayan wasu ɗan mintuna Dr Hasheem ya ɗago yana lalumen wayansa tunawa yayi ashe ya barta a gida daman bai fito da phone ba, miƙewa yayi ya fita waje kai tsaye wajen ma'ajiyin telephone ya nufa wanda kowa da kowa zaiyi waya a duk lokacin da yaso, number maigadin gidansa ya ƙira bugu biyu aka ɗauki ƙiran daga ɓangaren maigadi sallama yayi tareda tambayar waye ne? Dr Hasheem ne ya tambaye shi cewar "Ayushert tana gidan?..." maigadin jin muryar Ogansa ne yasa shi amsawa da sauri yace "eh ƙwarai tana ciki yanzu kam hala tayi bacci..." Dr yace "Okay duk wanda yazo karka buɗe saboda bazan samu damar dawowa gida ba, zan zauna agurin ƙanwata," daga nan ya katse ƙiran ya juya zai koma ɗakin da Lailah take.... *Ayushert* tana cikin flawowin gidan tana laɓe da akwatinta ta wajen bakin gate, tana jin wayanda Maigadi yake yi da Dr Hasheem ita damuwarta maigadi ya tashi daga gurin ta samu ta fice a gidan, ga ta ko ina hasken nepa ne, can tana tsaye sai taji maigadin yana faɗin "wayyo marata fitsari ya matseni da yawa, bari na ɗan zagaya nazo kuma na danna kwaɗo a gate nima na ɗan yi bacci na.." yana barin wajen kuwa Ayush tayi saurin buɗe gate ta fice tana jan akwatinta da sauri, daƙer ta samu napep a wannan daren ta nufi hospital yanda Junaid yake, suna isa asibitin kafin ta sauƙa daga cikin napep sai ga motar Malam Lawan ya fito daga cikin asibitin ya wuce cikin gari, fitowa tayi ta sallami mai napep sannan itama ta shige cikin hospital tana rurrufe fuska kamar wata marar gaskiya, ajiye jakarta tayi a guri guda tukun ta ƙarisa shige cikin compound ɗin hospital, lelleƙa ɗakuna ta shiga yi amma ta rasa a wani ɗaki aka ƙwantar da Junaid, wani ma'aikaci ne yayi mata magana ta bayanta yana cewa "Hajiya wa kike nema ne?.." juyowa Ayush tayi duk ta rufe fuskarta da mayafinta tace "am amm room ɗin da aka ƙwantar da Oga Junaid nake nema..." yace "Okay zo na nuna miki" yayi gaba itama tabi bayansa. suna zuwa wajen tayi saurin buɗe ɗakin ta shiga ganinsa tayi a ƙwance yana lumshe da ido alamar bacci yake, ga yanda aka ɗaura masa ledar jini a hannu, da sauri ta ƙariso gurin tana kuka tareda sa lallausar hannunta tana shafa masa fuskarsa, Junaid kamar a mafarki yake jiyo kukan Ayush, motsi ya fara yi a hankali yana ƙoƙarin buɗe idonsa, dasauri Ayush ta miƙe tareda shiga bayan labule ta ɓoye, buɗe eyes ɗinsa yayi ya juyo yanda yake jin kukan yaga ba kowa, ƙoƙarin tashi ya fara yi daiden lokacin da Malam Lawan ya shugo hannunsa riƙe da ledojin abun ciye-ciye, ganin Junaid yana shirin tashi ne yasa yayi saurin ƙarasowa yanda yake yana faɗin "lafiya kuwa Junaid? zaka gotar da alluran hannunka fah..." Junaid hannu yasa ya dafe kansa dake bala'in masa ciwo, duk anbi an zazzagaye kayin da bandeji cikin sassanyar murya yace "malam ina Yushert?..." girgiza kai malam Lawan yayi yana murmushi yace "Junaid kenam tin farkon farfaɗowarka kake ta tambayar Ayshert, yanzu ma kayi bacci ka tashi da sunan Ayshert a bakinka, shin meyasa bazakayi haƙuri ka danne zuciyarka ba..." Junaid ɗagowa yayi yana kallon Malam kamar zaiyi kuka yace "bazan taɓa cire Yushert a raina ba, haka kuma bazan taɓa rabuwa da Yushert ba, domin ita ɗin matata ce kuma jinin jikina..." Malam ne ya dafa kafaɗarsa tareda cewa "komai ɗan lokaci ne Junaid, idan kayi haƙuri Ayshert zata dawo gareka, a halin yanzu bazata fahimce ka ba, ka barni da ita Insha Allahu zata fahimce ka, inaso ka sani fa mahaifiyarka ta ɗaura muku Aure ne a ɓoye indai ba waɗanda aka ɗaura a gabansu ba babu wanda zai bada shaidar Aurenku, amma Alhamdulillah akwai shaidu da yawa waɗanda a gabansu aka ɗaura acikinsu har da ni da kuma abokin mahaifinka Barrister Aminu, kuma sannan ga katin shaidar Aure an bugosu tin a ranar, idan na samu zama da Ayshert zan sanar mata cewa tayi tunanin lokacin da Angela ta musulunta, a lokacin a gabansu nayi waya da Hajia Fateema akan batun Auren, ita marigayiya Maryam ta fara mun tambayoyi akan maganar Auren da nake yi da mahaifiyarka, tabbas da Maryam tana raye ita zata fahimtar da Ayshert toh amma nima zanyi iya ƙoƙari na domin Ayshert ba ƙaramin tsanarka tayi ba..." Junaid yana dafe da goshinsa yace "bani na kashe mata mahaifiyarta ba, wallahi bani bace! hasali ma in badan mahaifiyarta ba da yanzu bana raye a doron ƙasa, an kawo mun hali ta baya a daiden lokacin mahaifiyarta tazo ta shige tsakiya harin ya sauƙa akanta, ta ceci rayuwata, taya zan kashe ta? bayan Mahaifinta har dashi ya taya mu yaƙan babban maƙiyi tabbas ya taka rawar gani sosai, daga ƙarshe aka kamashi a matsayin mai laifi, shin taya zan bari ya cigaba da zama a matsayin mai laifin? Bayan yanzu na tabbatar shi ɗin ɗan uwan mahaifi nane, kafin na dawo Nigeria saida nayi silar fitowarsa daga cikin maƙarƙama, yanzu haka yana can cikin masarautar sa cikin ƙoshin lafiya, amma Yushert ta gagara fahimta ta tasa wuta a gidan mu ta ƙona mun mahaifiyata, da wanne zanji a cikin zuciyata, nasan ciwon raɗaɗin mutuwar mahaifiyarta ne yasa nima ta rabani da tawa farin ciki, shiyasa na danne ƙonar dake cikin zuciyata a yanzu burina shine Yushert ta dawo gareni ta yadda dani sannan ta maye mun gurbin mahaifiyata data rabani da ita, nima kuwa na maye mata gurbin data rasa, to ya zanyi mata..." ya ƙarasa maganar yana fashewa da kuka kamar wani yaro ƙarami... Ayush dake bayan labule itama kuka take ba tareda ta bari kukan ya fito ba, duk ta gama jin tattaunawarsu a zuciyarta take faɗin "na yarda dakai Yaya Junaid, na yarda dakai, amma bazan iya cigaba da zama dakai ba, ni na kashe maka mahaifiya taya zanji daɗin cigaba da tarayya dakai, nayi dana sanin aikata wannan zaluncin da nayi, nayi dana sani wayyo tirr dani! Mommy ta rufa mun asiri ta nuna mun kulawa kamar ƴar cikinta, Allah sarki matar arziƙi ki gafarce ni, na aikata babban kuskure a rayuwata, tabbas rayuwata bata da wani amfani..." ta toshe bakinta tana kuka ciki-ciki... Malam Lawan daƙer ya samu ya rarrashi Junaid sannan ya buɗe ledar daya shugo da ita, ya fitar da gasassun kaji ya baza masa su a cikin ledar, sannan ya buɗe masa lemuka na fata dana ruwa.. daƙer yake lallaminsa yake ci cikin nutsuwa da kulawa.. Ayush ƙamshin kajin ne yake kawo mata hari, kwata-kwata bata ƙaunar jin wannan ƙamshin, zuciyarta ne yake ta faman tashi, da sauri ta toshe bakinta da hannayenta biyu sakamakon aman da ya tsaya mata a maƙogaro, sai faman zazzaro ido take waje, yunƙurawa tayi ta ɗanyi wani ƙara kaɗan.. wannan ƙaran aman ne ya sauƙa akan kunnen Junaid, ɗagowa yayi yana waige-waige, Malam Lawan yace "lafiya kuwa?.." cikin sassanyar murya yace "ƙara naji, kamar wani yana cikin ɗakin nan..." murmushi malam yayi sannan yace "kai dai ba'a rabaka da mita, ni banji motsin kowa ba, kaide cigaba da cin abincin ka, so nake na samu na tafi gida idan ka kammala kaga yanzu ƙarfe 12 saura dare yayi sosai, amma ina tunanin barinka kai kaɗai.." Junaid idonsa akan malam yace "dare yayi kam malam yakamata ka koma gida, asibitin akwai security sosai, ba damuwa..." da murmushi a saman fuskar malam ya ɗan shafi gefen fuskar Junaid yana faɗin "shikenam zan tafi ka kula da kanka, Allah yayi maka Albarka.." Junaid jinjina kai kawai yayi yana kallon Malam har ya fice daga ɗakin... Bayan fitar malam ɗaukar ledar kajin yayi ya ajiye a gefe guda domin baya buƙatar cin komai, kawai malam ne ya takura masa akan yaci, har zai kishingiɗa ya ƙwanta kuma du ya sake jin yunƙurin amai, fasa ƙwanciyar yayi yakai idonsa saitin yanda yaji ƙaran, fincike kalurar hannunsa yayi sannan ya sauƙo daga kan gadon ya nufi gurin, hannu yasa ya yaye labulen ƙwatsam idonsa ya sauƙa akan Ayush wacce take tsaye duk ta ɓata kayan jikinta da amai, hannayenta dake toshe da bakinta suma amai ne yake gangarowa, ganin yanda Junaid ya zuba mata ido ne yasa ta wuce ta gefensa ta shige toilet, kai tsaye wajen sink ta nufa taje ta cigaba da ƙwarara aman da bai gama fitowa ba, Junaid ne shima ya shugo cikin toilet gaba ɗaya hankalinsa ya tashi jin yanda take ta yunƙurin amai kamar zata amar da kayan cikinta ga bata ci komai ba.. ji tayi ya dafa kafaɗunta biyu cikin sexy voice ya furta sunanta "Yusherttt..." itama ɗagowa tayi a hankali tana kallonsa ta cikin madubi idonta yayi lufu-lufu sun kumbura tsabar kuka, fuskar nan yayi jawur murya a sanyaye take magana "Ni ni bana son jin warin nama!, banason jin warin nama!..." juyar da ita yayi suna fuskantar juna yana kallonta cikin so da ƙauna, hannunsa yakai ta bayan rigarta ya soma zuge mata zip har zuwa ƙasa, ta saman kafaɗarta ya zamar mata da doguwar rigar har ƙasa ta zauna daga ita sai breziya da pant, haka suke kallon juna kamar zasu haɗiyi junansu daga baya Junaid yasa hannu ya rungumota kan faffaɗar ƙirjinsa ya manneta sosai da jikinsa yana shafar sumar kanta har zuwa gadon bayanta, yana cikin shafar bayanta ya ɓalle mata brezy, itama hannu tasa ta bayansa ta rungume shi tana kuka... Ɗaukar ta yayi sannan ya zaunar da ita a cikin farin bahon wanka ya kunna mata fanfo mai ruwan ɗumi saida ruwan yazo mata saitin ƙirjinta tukun ya kashe ruwan tareda ɗaukar sabulu mai ƙamshin gaske yana murza mata a jikinta cikin salo, haka yake bi yana mulmulka mata sabulun a duk ilahirin jikinta, lumshe ido tayi sannan ta ƙwantar da kanta a bakin bahon tana kallon sama, shima cire singet jikinsa yayi da gajeren wandonsa ya shiga cikin bahon dake baho ne mai girman gaske domin zai iya ɗaukan mutane uku zuwa huɗu, ƙara kunna musu ruwan fanfo yayi mai zafi har saida ruwan yazo saitin wuyansu tukun ya kashe, hannu yasa yana wanke mata jikinta ta ko ina daga sama har ƙasa daiden lokacin da ya rufu kanta a cikin ruwan ya manna mata kiss akan goshinta, still idonta a lumshe ko buɗe su batayi ba, sai daga baya ta buɗe idonta a hankali tana kallon cikin ƙwayar idonsa, hancin su yana manne dana juna haka numfashinsu yake hargutsuwa dana juna, a haka yake wanke mata jikinta a hankali yana shafar jikinta kamar wanda yake shafar jikin kifi tsabar tsantsi da laushi hannunsa yakai saitin pant ɗin ta ba tareda yasa hannunsa ta cikin pant ɗin ba haka ya soma shafar saman pant ɗin cikin salo, daiden lokacin ta sauƙe ajiyar zuciya tareda lumshe ido kamar mai yin bacci, haɗe musu lips yayi yana socking a hankali har ya zura harshensa cikin bakin ya kamo harshenta yana tsotsa kamar wanda ya samu lollipop, haka yake tafiya da hannunsa yana shafar tumbin cikinta har zuwa saman breast ɗinta, nan ma shafawa yake yana murzawa a hankali, gaba ɗaya ta gama fita hayyacinta haka itama take mayar da martani suna kissing junansu, ta zagayo da hannayenta biyu ta bayansa tana shafa shi itama a hankali, gurin yayi shuru sai motsin ruwa ake ji yana bada sauti a hankali, ƙara sauƙar da hannunsa yayi kan tumbin cikinta yana shafawa a hankali ji yayi kamar ba tumbin Ayush yake shafawa ba domin yasan kalar tumbinta ɗan ƙarami ne a shafe kamar babu komai a cikin cikinta, yanzu kuma yaji tumbinta ya sauya sosai cikin ya ɗan yi girma sannan yayi tauri, raba lips ɗinsu yayi sannan ya ɗago yana kallonta cikin wani irin yanayi a hankali ya ambaci sunanta "Yushert.." Itama buɗe eyes ɗinta tayi a hankali take binsa da kallo cikin sexy voice yace "you have a pregnant?..." zaro Ido tayi sosai tana binsa da kallo, murya a sanyaye ya kuma cewa "Please ki gaya mun gaskiya my wife, cikin ki ya ɗago sosai..." girgiza masa kai tayi babu bakin magana, zuciyarta ne yake wani irin bugawa, ta tsorita sosai jin abunda ya faɗa, Junaid hannunsa yakai ƙasin marar ta yana shafawa a hankali yake motsi da lips ɗinsa yace "marar ki ya ɗago Yushert, kina ajiye da Baby na.." ya ƙarasa maganar yana goga musu hancinsu guri ɗaya, ji yayi tace "tayaya hakan zata faru?..." ɗagowa yayi yana kallonta da murmushi a fuskarsa yace "our first night, kafin na tafi California shin kin tuna? kinsan lokacin ma an ɗaura mana Aure..." Ayush rufe idonta tayi sosai tana tariyo abunda ya faru a tsakaninsu, a cikin zuciyarta take maganar cewa "kenam daga yi sau ɗaya sai ciki? Impossible I can't believe..." a daiden lokacin Junaid ya manna mata kiss a saman lips ɗinta... tashi yayi Junaid daga kanta yana faɗin "rufe idonki kar ki sake suma mun irin na wancan lokacin farkon zuwanki gidan mu..." Ayush ganin yana shirin miƙewa a tsirararsa yasa ta rufe idonta ta sauri, har saida ya fita daga cikin bahon ya ɗauki 3quater sa ya zura, jikinsa duk damshin ruwa yasa hannu yayi wa Ayush ɗaukar luɗa ya fita da ita cikin room ɗin da yake a asibiti, ƙwantar da ita yayi sannan yasa hannu ya cire mata jiƙaƙƙen pant ɗinta ya jawo mata mayafi ya rufe mata jikinta gaba ɗaya, har yayi wannan ɗawainiya idonta a rufe yake, komawa cikin toilet yayi yaje ya wanke mata kayan sakawarta daya ɓaci da amai har pant ɗinta da breziya duk saida ya wanke su tas sannan ya shanyasu, ɗaukar singlet ɗinsa yayi ya sanya shi a jikinsa sannan ya koma cikin ɗakin, saida yasa key a ɗakin tukun yazo shima ya ƙwanta tareda rungumo Ayush jikinsa ya rufa musu mayafi kafin a ƙirga mintuna har bacci yayi awun gaba dasu.... Asussuban farko Ayush ta tashi daga bacci tana mutsil-mutsil jin yanda Junaid ya ƙanƙameta ne yasa ta ɗanyi shuru saboda kar ta tashe shi, a hankali take zamar da hannunsa daga rungumar da yayi mata, da haka har tayi nasarar tashi ba tareda ya farka ba, duban kanta tayi taga ashe tsirara take ƙwance, da hanzarinta ta nufi toilet taje ta saka kayanta sannan ta fito tazo gaban Junaid ta durƙusa tana hawaye a hankali take faɗin "kayi haƙuri Yayana nima na sani ina ɗauke da cikinka na tsawon wata huɗu, amma sai dai a wannan lokacin bazaka kasance tareda mu ba, dani da jaririna zamuyi nesa dakai saboda bamuyi maka halacci ba, munci amanarka, jaririna a jikina yake dole zai kasance dani a koda yaushe, Yaya Junaid daga yau bazaka ƙara ganin mu ba, ina fatan Allah ya baka wata matar da ta fini komai, kuma Allah ya baka ƴaƴa masu albarka waɗanda suka fi jaririna, ina sonka mijina...." tana kaiwa ƙarshe ta miƙe tareda kai masa sumbata akan goshinsa daga nan ta nufi bakin ƙofa a hankali ta murza key ta buɗe tayi ficewarta, tana fita daga cikin asibitin ta fara gudu ko tsaya ɗaukar akwatinta batayi ba, haka ta wuce security tayi ficewarta, Garin shuru ba kowa sai hasken nepa ta ko ina, wani wajen kuma duhu ne ba haske da haka take tafiya ƙafarta ko takalmi babu, wani mai mashin ne ya tsaya a gefenta yana faɗin "Hajia lafiya kuwa na ganki a cikin daren nan ko asuba ba'a ƙira ba.." juyowa tayi tace "lafiya ƙalau wani warai mai ɗan nisa nake son zuwa.." yace "toh idan babu matsala hau na kai ki yanda zaki sauƙa, Allah yasa dai ba aljana zan ɗauka ba..." Ayush kuka take jin abunda ya faɗa ne yasa ta yin dariya ta hau mashin suka tafi, tafiya suke ba ƙaƙƙautawa har sun fara fita daga cikin gari babu wasu gidaje sai jeji, Mai mashin ne ya tsayar da mashin yana faɗin "dan Allah baiwar Allah wallahi da niyar temako na ɗauko ki naga kina cikin matsala, nima asibiti zanje dubowa mahaifiyata dan Allah karki cutar dani, yanzu na gane cewa ke ba mutum bace amma ki rufa mun asiri ki barni na koma cikin garin mu lafiya, wallahi daga nan bazan ƙara yin gaba ba, wallahi ni ko fuskarki bana iya gani tsabar duhu sai iya hasken mashin ɗinane kawai..." Girgiza kai Ayush tayi tace "shikenam ba damuwa hakan ma nagode sosai, ka juya kawai ni zan ƙarisa gurin da zanje..." tana kaiwa nan tayi gaba abunta ko tsoro da fargaba babu niyarta shine ta koma jejin da suka zauna da mahaifiyarta... Shi kuwa mai mashin da gudu ya juya ya koma baya.. Bayan sallar asuba gari yaɗan fara wayewa Junaid yana ƙwance bai tashi ba har yanzu domin wani irin nannauyar bacci ne ya ɗauke shi, yana cikin bacci yaji an turo ƙofa da ƙarfi Malam Lawan ne ya shugo da hanzarinsa yana ƙiran sunan Junaid, "Junaid! Junaid!! Kai Junaid ka tashi mana" Mutsil-mutsil Junaid yake yana shirin buɗe idonsa, malam Lawan ne yasa hannu ya finciko shi zaune yana faɗin "ko sallah bakayi ba, shin kasan maiyake faruwa ne yanzun?.." Junaid waige-waige ya somayi yana faɗin "ina Yushert take?.." malam yace "Ayshert kuma tazo ne?.." cikin rashin fahimta malam yake kallon Junaid, Junaid ganin kar malam yayi tunanin wani abu yasa ya kawai da maganar Ayush yace "lafiya kuwa malam?.." Malam yace "mafarki kayi koh?.." sunkuyar da kai ƙasi Junaid yayi yace "Hmmm!.." Malam yace "yanzun tashi kayi sallah tukun kaji wani zance.." sauƙa daga kan gadon Junaid yayi yana tunanin abubuwa da dama a ransa ya nufi toilet ya ɗauro Alwala, yana maganar zuci "shin ina Yushert taje? yaushe ta tafi? daman ba zuwa tayi ta zauna dani ba?..." haka yake wannan tunanin har ya komo ɗakin ya ɗauki jallabiyarsa yasa sannan ya daidaita nutsuwarsa ya fara sallah, bayan ya idar ya fuskanci malam Lawan yaga kamar yana cikin matsala yace "wai malam meyake faruwa ne kam?..." Malam ne ya miƙe tsaye yaje ya ɗauki remote ya kunna plasman dake manne a jikin bangon ɗakin yace "Junaid kalli abunda yake faruwa..". Tashar labarai ne ta ko ina ana maganar Ayush cewar ita tasa wuta a gidan Doctor Fateema, ita tayi sanadiyar mutuwar Doctor Fateema, ga photunan Ayush yanda yaketa yawo ana nunota ga kuma photon marigayiya Doctor Fateema, ga photon gidan yanda yayi ƙurmus, an bayyanar cewar Ayush tana nan a gidan Doctor Hasheem a ɓoye.. Sai kuma aka nuno video gidan Doctor Hasheem yanda mutane suka taru a ƙofar gidansa kowa yana riƙe da makamai ga ƴan jaridu ga sojoji da ƴan sanda dasu human rights duk a ƙofar gidan, a cikin television ganan maigadin gidan yanda aka cire masa kayan jikinsa a barshi daga shi sai gajeren wando ana tilasta masa akan ya faɗi yanda Doctor Hasheem ya ɓoye Ayush.... Kawar da wannan video akayi suka kunna recording maganar Ayush yanda ta amsa da cewa ita ta ƙona Doctor Fateema a lokacinda take magana da Doctor Hasheem duk a cikin television yanzu ta tabbata cewar ita ta kashe Doctor Fateema ta hanyar dasa gobara a gidanta.... Junaid yana zaune baisan lokacin da ya miƙe tsaye ba kamar zai haɗiyi ransa, a fusace yace "waye ya sanar da ƴan jarida wannan maganar? Waye yayi wannan aika-aika? bazan zauna ba dole zan nemo Yushert bazan bari a raunanata ba, tana da juna biyu a jikinta..." a tsawace yake wannan maganar ya fice daga cikin ɗakin a ruɗe, Shima Malam tashi yayi yabi bayansa da sauri, suna zuwa Malam ya buɗewa Junaid motar shima ya shiga suka tafi, kai tsaye gidan Doctor Hasheem suka nufa yanda ƴan jaridu da sojoji suke... Shima Doctor Hasheem yana daga hospital yaga yanda mutane suke kallon labarai a babban television cikin hospital ko tsayawa sauraro baiyi ba ya fice da gudun gaske yana ambaton sunan "Ayush" motarsa ya shiga a ɗari yabar asibitin ya nufin gidansa... *TOPAH LABARI YANATA TAFIYA..* *WAI ME AYUSH TAKE NUFI NE🤔? SHIN DA JARIRIN MU ZATA KOMA JEJI KENAM🙄 GASKIYA JARIRIN MU BAZAIYI IRIN RAYUWAR DA TAYI ACIKIN JEJI BA YACIINN😳😳* 𝑡𝑦𝑝𝑖𝑛𝑔✍️ 𝗠𝗔𝗧𝗔𝗥 𝗗𝗔𝗠𝗨𝗦𝗔 the wife of a tiger🐅🐅🐅🐅 𝙼𝚊𝚕𝚕𝚊𝚔𝚒𝚗 𝙰𝚜𝚖𝚎𝚎𝚝𝚊𝚑 ✍️✍️ 𝙿𝚊𝚒𝚍 𝚋𝚘𝚘𝚔 𝚌𝚊𝚕𝚕 𝚘𝚛 𝚠𝚑𝚊𝚝𝚜𝙰𝚙𝚙 09065443871 *💫💫{{N W A}}💫💫* Book two C̶h̶a̶p̶t̶e̶r̶ 47 ➡️ 48 *FOREST* tin da safe Ayush take faman haɗa ɗakin kara har zuwa yanzu bata ƙarisa ba, dajin babu motsin kowa sai zallan kukan tsuntsaye, ata kusa da ita kuma bishiyoyin mangoro ne da su kashu, idan kayi tafiya kaɗan kuma rafine daga nesa zakaji ƙarar tafiyan ruwa, ga zunzurutun sanyi da iska da akeyi amma da haka take wannan aikin... Ta ɓangaren su Junaid kuma bayan isowarsu gidan Doctor Hasheem da sauri ya sauƙo daga cikin motar kai tsaye ya miƙi hanyar shiga cikin gidan, ƴan jaridu ne suka yo kansa da gudu suna masa magana akan ya faɗa musu abunda yake cikin ransa da kuma kalar hukuncin da zai ɗauka akan yarinyar, Junaid ganin sun tare masa hanya kuma ga jerin tambayoyin da suke masa yasa ransa ɓaci sosai a fusace yasa hannu ya hankaɗasu baya yana faɗin "stay away from me, stupid people's.." Duk ƴan jaridun nan faɗuwa ƙasi sukayi a tsorace suka miƙe suna guduwa, shiga cikin gidan Junaid yayi yana ƙwallah ƙiran Ayush, "Yushert! Yushert!! Yushert!!! ki fito babu abunda zai sameki, ina tareda ke..." wani Ma'aikaci ne ya biyo bayansa yana faɗin "yallaɓai bata gidan fa duk mun dudduba, ina tunanin Doctor Hasheem ya ɗauketa sun gudu..." a firgice Junaid ya juyo yana kallon Ma'aikacin ido a zazzare yace "Whatttt?..." juyawa yayi da gudunsa ya fita daga gidan yana fita ya tarar da Ogansu na Sojoji shima yazo wajen, nufa gurin Ogan yayi yaje gabansa yana faɗin "Please Oga kuyi haƙuri kubar mun aikin nan a hannuna, kace wa duk sojojin su tafi kar su saka kansu cikin wannan case, Please..." Oga murmushi yayi yana kallon Junaid yace "Captain Junaid Wannan case ɗin bai shafeka ba, Ni General nace ka cire hannunka akan wannan case, ka bar mana komai a hannun mu tinda kai baka kishin mahaifiyarka, bawai zamuyi aikin nan saboda mahaifiyarka bane no zamuyi ne saboda mu kare hakkin ƙasar mu, bazamu lamunci wannan zaluncin da yarinyar nan tayi ba dole hokum tayi aiki akanta, kuma ko waye yayi ƙoƙarin aikata wannan laifin sai mun hukunta shi, balle a aikata wannan ƙazamin hukunci akan mahaifiyar Captain kuma muna ji muna kallo mu ƙyale no impossible, kuma ko kaine ka aikata hakan dole mu ɗau hukunci akanka! You Understand?" Junaid gyara tsayuwarsa yayi yace "Yes Sir..." tareda sara masa... General karɓan lasfika yayi yana sanarwa akan cewar "Sojojin mu inaso kafin zuwa gobe ku tabbatar kun kamo yarinyar nan duk yanda ta shiga, da zaran kun kamota ku tabbatar kun miƙata hannun hukuma daga nan a kaita Kotu a yanke mata hukunci daidai da ita, idan kuma taƙi kamuwa da zaran kun ganta ku harbeta wannan umarni nane..." yana kaiwa nan ya shige motar suka bar wajen da sauran motacin sojojin da suka zo a tare... Junaid yana tsaye zuciyarsa sai faman bugawa take, gaba ɗaya ya tsorita da jin kalaman General, yana kuma tunanin taya akayi maganar nan ta fito waje har kowa ya sani? "Shin waye ya tona wa Yushert asiri kuma harda ɗaukan video ba tareda saninta ba? ina zargin mutane biyu! Hasheem ko Lailah..." yana ƙarasa maganar saiga Dr Hasheem yazo shima da motarsa, dasauri ya fito daga cikin motarsa yana mamakin ganin yanda aka taru a ƙofar gidansa, ga motar sojoji gana police ga kuma ƴan jaridu, Da gudu Junaid yayo kansa yaci ƙwalar rigarsa yana faɗin "where is my Yushert? Ina ka kaimun ita?..." Dr Hasheem ƙoƙarin zamewa yake yana cewa "Ni kuma? rabona da ganin Ayushert tin jiya ai.." kafin Dr Hasheem ya ƙarasa maganar Junaid ya haɗe musu goshi da ƙarfin gaske ya gwara kansa dana Dr Hasheem har saida ya kifu a jikin motarsa ɗagowa yayi yana kallon dishi-dishi tsabar buguwar da Junaid yayi masa, Junaid ɗago shi yayi ya fara kai masa naushi yana tambayarsa "ina Yushert? where is her Ina ka kaita?..." yana tambayarsa amma bai daina dukansa ba, haka ya rinƙa kwaɗa shi da ƙasa yana ɗagoshi.... Ƴan jaridu duk sun saita camerar su kan Junaid duk yayi wa Dr Hasheem jinajina, sannan duk wanda yayo kansa zai ceci Hasheem haɗasu yake ya mazgesu tare, shiyasa duk aka rasa wanda zaije ya karɓi Dr Hasheem, haka sojojin nan duk tsoron Junaid suke shiyasa suma suka make a guri ɗaya babu wanda yazo kansu, Malam Lawan ganin Junaid yana shirin yin kisan kai ne yasa ya nufi gurin da yake da sauri yana faɗin "kai Junaid kanada hankali kuwa? ka barshi haka mana..." Malam Lawan ne ya rirriƙe shi Junaid a fusace ya dunƙule hannunsa zai kaiwa malam naushi dake bayansa, ganin malam ne yasa ya fasa Lokaci guda kuma ya durƙusa a ƙasi yana kuka.... Maganganun General ne suke masa yawo a ƙwaƙwalwa, Ga kuma Dr Hasheem a yashe a ƙasi yanata birgima, jini ta ko ina fita yake, duk Junaid ya faffasa masa hanci da baki ga idonsa yanda ya kumbura suntum tsabar naushin da aka kai masa a gurin, wasu Police ne su uku suka zo gurin da Dr Hasheem yake a ƙwance suna ƙoƙarin ɗaga shi, Junaid yana durƙushe da gwiwowinsa ya ɗago da dara-daran idanuwansa waɗanda suka kaɗa sukayi jawur tsabar baƙin ciki a tsawace yace musu "ina zaku kaishi?..." wani daga cikin ɗan sandan ne yace "am amm yallaɓai daman zamu kaishi ofishin mu ne zamuyi wasu bincike akansa ne sakamakon ya ɓoye mai laifi..." Kafin yakai ƙarshen maganarsa Junaid ya darara masa uban tsawa yana faɗin "police station ɗin banza! Ina sojojin mu suke?..." da gudu sojoji suka yo kan Junaid suna sara masa tareda faɗin "Yes Sir..." cikin ɓacin rai yake magana yace "ku tafi dashi can headquarter kuyi ta dukansa har saiya gaya muku yanda yakai Yushert, idan kuwa bai gaya muku ba ku ƙwaƙule masa idanuwansa gaba ɗaya umarni nake baku ba shawara ba..." gaba ɗayansu hannu suka kai saitin goshinsu suna faɗin "Yes Sir an gama..." haka suka ɗauki Dr Hasheem kamar babu rai a jikinsa suka sashi a motar suka nufi headquarter... wani ɗan jarida ne ake masa video yanata surutai akan abubuwan da suke faruwa, a fusace Junaid ya juyo ya wurga masa wani ƙaton dutsi akan goshinsa, a razane ɗan jarida yayi ƙara game da sa hannu yana dafe da goshin kafin kace mai goshi ya fashe nan danan jini ya wanke masa fuska, Ganin haka duk ƴan jaridun suka fara gudu suna shiga motocinsu, shima wanda aka fasawa goshin tinin ya shiga motar sun gudu, suma ƴan sandan gurin kama hanya sukayi suka tafi, kowa ya watse ya rage daga Malam Lawan sai shi Junaid ɗin, daƙer Malam Lawan ya rarrashi Junaid akan ya tashi su koma gida, zuciyarsa ne yake wani irin tafarfasa da haka yake jan ƙafa ya buɗe murfin motar zai shiga ƙwatsam sai yaji ana ƙiran sunansa ta baya "Ogah Junaid! Ogah Junaid!! ga wannan jakar mun sameshi ne a cikin asibiti..." wani ma'aikacin asibiti ne ya kawo masa, Junaid hannu yasa ya karɓi akwatin cike da mamaki yace "wannan ai akwatin Yushert ne" yana cikin wannan tunanin yaji likitan yace "ga wannan takardar a jikin akwatin muka ganshi..." Junaid karɓa yayi idonsa akan likitan, Likitan ganin irin kallon da Junaid yake masa ne yasa shi tsarguwa ya fara yin dariyan yaƙe yana faɗin "am saidai Ogah ban karanta saƙon ba wallahi, naga a bayan takardar an rubuta sunanka da manyan baƙi shiyasa nace wannan saƙon naka ne..." yana kaiwa ƙarshen maganar ya juya da sauri ya tafi, Junaid mota ya shiga malam Lawan ya jasu suka tafi... Bayan isar su Junaid gida zama yayi a bakin gado yana karanta rubutun jikin takardar, abunda Ayush ta furta wa Junaid a yayin da yake bacci kafin ta tafi shi ta ƙara maimaita wa ajikin takardar!! Junaid ba ƙaramin tashin hankali ya shiga ba har da ƙwallarsa a hankali ya furta "why Yushert meyasa zakiyi mun haka? ke da yarona bansan halin da zaku shiga ba, ya zama dole na nemoku a yanda kuke...." tashi yayi ya fara tattara kayansa ya shirya duk wasu abubuwansa ya haɗesu a cikin jakarsa, sannan ya shiga wanka shaf-shaf ya fito yayi shirinsa a nutse, yana sanye da blue jeans da t-shirt mai zanen White and blue, da blue cover shoe a ƙafarsa, yana tsaye a gaban mirror yana taje suman kansa daya ƙwanta luf-luf zuwa kafaɗarsa, ga ya gyara sajen fuskarsa shima ya ƙwanta har gemunsa kamar wanda ya wanke da shampoo gashin yayi baƙi ƙirin ga laushi, farinsa kuma saiya ƙara fitowa sosai ba karamin kyau yayi ba, ɗaukan turare yayi mai shegen ƙamshi yana feshe duk ilahirin jikinsa dashi, Daiden lokacin malam Lawan ya shugo da tray ɗin abinci a hannunsa ganin Junaid yanata shiri kamar wanda zai bar ƙasar yace "ha'a mutumin ina zuwa ne haka naga ka fitar da akwatuna lafiya dai koh?..." Junaid ƙarasowa gaban malam yayi ya karɓi tray ɗin hannunsa ya ajiye a saman table ya ɗago yana kallonsa da damuwa a fuskarsa, Malam Lawan kansa a ɗage shima yana kallon Junaid, domin Junaid ba ƙaramin tsayi ne dashi ba, duk da malam Lawan nada tsayi amma bai kai kafaɗar Junaid ba, asalin sangami ne ga ƙiran jikin ƙarfi, duk jikinsa a mummurɗe babu alamar tamowa ajikinsa😜 Yace "malam kayi haƙuri bazan iya zama anan gidan ba, inaso zan koma ɗaya daga cikin gidaje na, tin shekaran jiya nasa aka gyara mun gidan da zan zauna, saboda haka yanzu inaso zan koma ne, kuma acan ni kaɗai zan fi jin daɗin gudanar da aikina! Nagode sosai malam, ka bani kulawa yanda ya kamata..." Malam yace "toh shikenam Junaid ba laifi amma kafin ka tafi ka zauna kaci abinci ko..." taɓe fuska Junaid yayi sannan yace "gaskiya bana jin zan iya cin komai a halin yanzu, idan akwai milk shi nake buƙata..." Malam Lawan da hanzarinsa ya nufi gurin tray ɗin abinci yana faɗin "eh akwai mana bari na haɗa maka..." ***** *AFTER 30 DAYS* Ayush ce take tsaye a jikin bishiyan mangoro da wani dogon ice a hannunta sai faman tsalle take tana son ciran mango🥭, tayi nasarar ciran guda biyar ana shida ne ta soma jin gurnani ta bayanta, tsayawa tayi tana ƙoƙarin juyawa a hankali, idonta ne ya sauƙa akan wani ƙaton kura yana fuskantar ta, a tsorace ta soma ja da baya juyawa tayi da gudun gaske shima kuran bin bayanta yayi yana binta da gudu itama gudu take har ta iso saitin ɗakin da take zaune tana zuwa ta ciri wani ƙaton mashi mai tsayin gaske kafin ta ankara kuran yayi sufa yakai mata yakushi, buɗe baki yayi zai kai mata cizo a gigice tayi ihuu tare da kai mashin nan cikin bakinsa ta caka masa har saida mashin ya fito ta bayansa, faɗuwa kuran yayi ta gefen ta yana shure-shure ga jini yanda yake fitowa ta bakinsa, itama Ayush ƙwanciya tayi ta gefen kuran tana maida numfashi hannunta kuma akan tumbin cikinta wanda ya fara girma tana jin yanda cikinta yake ta motsawa da ƙarfi tana jin raɗaɗin hakan jurewa kawai take idonta a lumshe, Bayan ta ɗan huta kaɗan ta tashi ta maida mashinta yanda yake a ajiye sannan ta fara jan kuran nan har saida ta kaishi can nesa da ɗakinta ta jefashi cikin wani ƙaton rami ta juyo tana jan ƙafa daƙer domin ba ƙaramin gajiya tayi ba, zuwa tayi ta ɗauko mangwarayenta ta dawo ɗakinta, Ayush haka take rayuwa a cikin dajin nan ita kaɗai, duk ta cire tsoro da fargaba a ranta gani take zata iya tinkarar kowa duk wanda yace zai kawo mata farmaki mutum ko dabba, Abincinta daga mangoro sai kashu sai kuma ayaba da wasu kayayyakin itacuwa wanda baza'a rasasu acikin jejin ba, Ruwa kuwa tana kusa da rafi takan je ta ɗebo ruwa a cikin jarkan ta kawo ɗakinta na kara, cikin ɗakinta kuwa babu komai in banda bunannaki data haɗa gado dasu ta shimfiɗa mayafinta take ƙwana akai, Ga cikinta kuwa yanzu yana 5months.... ****** A ɓangaren Ogah Junaid kuwa ba yanda bai shiga neman Ayush ba amma ko labarin ta babu, cikin dare bai hanashi fita nemanta ba, haka ya ƙauracewa bacci saboda Ayush, ya shiga cikin damuwa sosai, Haka sauran sojojin da akasa su nemo ta suma babu wani labari akanta, Shi kaɗai yake zaune a gidansa babu kowa sai iya wani ƙarfaffan maigadi daya nemo sai kuma karnuka daya zuba a cikin gidan waran su uku irin buzajen nan na ƙasar waje, gidane haɗaɗɗe wanda aka tsara shi, falon gidan ma abun kallo ne balle idan ka haura can upstairs mai hawa na biyar nan ne ɗakin Junaid tsararren ɗaki na alhurma, (gaskiya idan nace zan tsaya tsara kyan gidan zamu ɓata lokaci ne...) yana zaune a bakin gadonsa ya dafe kansa da hannu biyu yana kallon ƙasi duk abun duniya yabi ya isheshi, tunanin Dr Hasheem ne ya faɗo masa a rai wanda yake can a hannun sojoji a zabure Junaid ya miƙe tsaye yana faɗin "na manta da wancan mutumin tsawon wata guda yana headquarter ya kamata naje na sallame shi..." yana kaiwa nan ya yi ficewarsa... Doctor Hasheem yana zaune shi kaɗai acikin gadurum na sojoji ya zama abun tausayi, duk wanda ya ganshi saiya zubar masa da hawaye, Gaba ɗaya an canza masa kamannunsa, fuskan nan ya kumbura sosai! leɓɓerin bakinsa yayi dogo kamar bakin kare tsabar naushin hannun gardawa daya sha, idanuwansa sunyi fusu-fusu sun kumbura sosai don daƙer yake iya buɗe eyes ɗinsa, sun ƙaramce sunyi ciki sosai tsabar kumburi, gefen fuskarsa ɗaya yafi ɗaya kumbura ɗayan ɓangaren fuskarsa ta dama yanda kasan an hura filfila tsabar kumburi, hancinsa ya baje ya zama ƙatoto tsabar naushi, wani irin rashin mutunci ma da suka tashi yimasa sai suka haske masa kayinsa gaba ɗaya sukayi masa malu tanɗal yanda kasan madubi haka kayin yake sheƙi ga sun faffasa masa kayi duk ya kumbura, (Allah Sarki Dr Hasheem Allah zai saka maka wallahi😭😭)... Bayan Ogah Junaid ya iso zuwa yayi ya zauna akan kujerunsu ya ɗora ƙafarsa ɗaya akan table dake gabansa yana jingine da jikin sofa, wasu sojojin suna zaune a wajen wasu kuma sunata kai kawo a wajen, Junaid idonsa a lumshe ya ƙira sunan ɗaya daga cikin yaransa sojoji yace "kaje ka tafo mun da wancan mutumin dake kulle ka kawo mun shi yanzu..." wanda aka aika ne ya gyara tsayuwarsa sannan ya sara masa tareda faɗin "Yes Sir..." daga nan ya tafi da saurinsa, ɗaya daga cikin manyan sojojin wajen ne wato canal Ahmad yana fuskantar Junaid yace "wato Oga Junaid Wannan gayen ba karamin buguwa yasha ba, har na tausaya masa wallahi kuma shegen yaƙi faɗan gurin da yarinyar take..." Sergeant Adams ne ya ari bakin Canal yana faɗin "toh daman akwai wanda zai shugo cikin headquarter ya fita lafiya ne?..." Captain Junaid gyara zamansa yayi yana fuskantar su sannan yace "wannan mutumin gaskiya yake faɗa bai san yanda yarinyar nan take ba, na daɗe da sanin hakan just na rabu dashi ne saboda dalili ɗaya..." Canal yace "toh amma kasan da hakan kuma ka barshi aka raunana shi haka?..." Captain Junaid murmushi yayi yana motsi da lips ɗinsa a hankali cikin sassanyar murya yace "na tsani raini a rayuwata, hannu yasa ya daki Captain ɗin sojoji, shine dalilin dayasa na ƙwanta akan gadon hospital, but a lokacin na kyale shi ne because of my partner of mind...." ya ƙarasa maganar yana cije lips ɗinsa, Sergeant ne ya zabura ya miƙe yana faɗin "whatt? Ogah shine tin a lokacin baka sanar mana mun dagargaza masa ƙwaƙwalwa da bullet ba, kutt gaskiya ya gama rainaka Ogah..." Captain Junaid ya sake yin smile yace "no na ƙyale shi ne saboda girman Abokantaka tin yarinta amma in badan haka ba da tinin na yanke masa hannayensa duk biyun..." Canal yace "gaskiya sai an ƙara hukunta shi domin abu ne mai wuya ace mutum yasa hannu yayi kokuwa da solder, solder ma babba acikin sojoji impossible..." Commander Nazif dake zaune sai faman chatting yake duk yana jin tattaunawar da suke yi sai a wannan lokacin ya ɗago yana faɗin "toh shi Captain ina yake gani har ayi masa dukan da za'a ƙwantar shi a gadon asibiti? kodai daman hurarin banza ne babu ƙarfi...." ya ƙarasa maganar yana tintsirewa da dariya, haka sauran sojojin wajen suma suka fara dariya... Oga Junaid a fusace ya wurga masa key ɗin motar hannunsa ya miƙe tsaye yayo kan Commander yana shirin kai masa naushi! a ruɗe Commander ya riƙe hannun Junaid yana faɗin "Please and please forgive me our Ogah, nayi kuskure..." fasa naushinsa yayi ya hankaɗa shi ƙasi ya faɗi daga shi har kujerar, Junaid kallon sauran yayi yana nuna su da yatsa yace "ku kiyaye ni wallahi, idan na rikice muku bazaku gane kaina ba..." haƙuri suka soma bashi suna faɗin "sorry Oga tiger we'll not try to hurt you again, please colm down! colm down!! colm down!!!..." Junaid ransa a ɓace ya zauna yana huci daiden lokacin aka kawo Dr Hasheem, Junaid juyawa yayi yana binsa da kallo da farko baiyi tunanin Dr Hasheem bane saida ya ƙareshi da kallo tukun ya iya gane shi, Junaid miƙewa yayi tsaye yana faɗin "meye wannan nake gani?..." Sojan daya kawo Dr Hasheem ne yace "Oga mutumin da kace ayita dukansa nan ne..." Junaid taɓe baki yayi yace "kuma sai nace ayi masa rauni har haka?.." Junaid ƙare wa Dr Hasheem kallo yake tin daga sama har ƙasa gaba ɗaya sun faffasa masa jiki tsabar duka da sanda, ga gefen kunnensa tabo guda ya fashe wannan fashewar gurin wani ne daga cikin sojojin ya maka masa waren ƙarshen bindiga a wajen kunnen, yana tafiya yana ɗingishi sun gurɗe masa ƙafa baya iya tafiya sosai, Girgiza kai Junaid yayi sannan yace "ina Lailah?..." Dr Hasheem daƙer yake motsa bakinsa tsabar ciwon da yake masa, baki yayi tsayi sai jinin dake burtsowa a hankali yace "tana asibitin Doctor Mansur..." "meya faru da ita?..." Junaid ne yayi tambaya cike da mamaki domin yanaso ya kamota yayi mata hukunci daidai da abunda ta aikata domin ya rigada ya binciko itace ta watsar da duk bayanan Ayush wa ƴan jaridu.... Dr Hasheem fashewa yayi da kuka mai cin rai.. Junaid ne yazo kusa dashi yana faɗin "it's okay no anything can happen to you okay..." yana rarrashinsa yasa hannu ya ɗauke shi a saman kafaɗarsa suka nufi hanyar waje, Junaid yana jin ɗaya daga cikin sojojinsu yana faɗin "ai wannan hukuncin mai sauƙi mukayi masa da sauran kaɗan mu yanke masa sawayensa ai..." Junaid ko kula shi baiyi ba, fita waje yayi ya buɗe murfin motarsa ta baya ya saka Dr Hasheem sannan shima ya shige ciki lokacin wani sojan ya fito yana cewa "Oga! Ogah ka manta key ɗin motar..." karɓa yayi sannan yaja motar suka tafi, Kai tsaye Asibitin da aka ƙwantar da Lailah suka nufa daga nan shima Doctor Hasheem za'a duba lafiyarsa...... *ALLAH SARKI DOCTOR HASHEEM ƊINAAA😭😭😭* *JUNAID KAI DA SOJOJINKA ALLAH YA ISAN MU...* 𝑡𝑦𝑝𝑖𝑛𝑔✍️ 𝗠𝗔𝗧𝗔𝗥 𝗗𝗔𝗠𝗨𝗦𝗔 the wife of a tiger🐅🐅🐅🐅 𝙼𝚊𝚕𝚕𝚊𝚔𝚒𝚗 𝙰𝚜𝚖𝚎𝚎𝚝𝚊𝚑 ✍️✍️ 𝙿𝚊𝚒𝚍 𝚋𝚘𝚘𝚔 𝚌𝚊𝚕𝚕 𝚘𝚛 𝚠𝚑𝚊𝚝𝚜𝙰𝚙𝚙 09065443871 *💫💫{{N W A}}💫💫* Book two C̶h̶a̶p̶t̶e̶r̶ 49 ➡️ 50 Bayan isar su Junaid asibitin da aka ƙwantar Lailah, kai tsaye room 8 suka shiga da wani Doctor wanda ya rakosu har ɗakin da Lailah take, ganin ta sukayi akan gadon tana zaune ta naɗe sawayenta kamar mai cin tuwo, ido a rufe tana ta jujjuya hannayenta biyu tana wasu surutai marasa kan gado, Doctor Hasheem ne ya nufo gurinta da gudu yana ambatar sunanta haɗe da kuka yake faɗin "Lailah! Lailah ki dawo hayyacinki dan Allah, haba Autar mama da Abba..." kuka ne yaci ransa sosai yana rungume da ita, Shi kuwa Junaid yana tsaye ya zuba musu ido, ganin Lailah a cikin wannan halin ba ƙaramin tausaya mata yayi ba, suna cikin wannan halin saiga babban likita ya shugo wato Doctor Mansur, zuwa gefen Lailah yayi ya zauna yana faɗin "please Doctor Hasheem ka daina kukan nan kar ka hargutsa mata lissafi.." Dr Hasheem ɗagowa yayi da rinanan idanuwansa yana riƙe da hannun Lailah yace "Doctor ba yanda za'ayi Lailah ta dawo hayyacinta?..." Doctor Mansur ne ya dubi Dr Hasheem yace "kaima ai kana buƙatar dawowa hayyacinka, ka duba kaga yanda ka dawo Dr Hasheem? kamar ba kai ba, dubi fuskarka kamar dattijon biri, Ni tinda ka ajiye Lailah a asibiti tsawon ƙwanaki baka dawo ba na shiga ƙwanƙwanto sai daga baya aka cemun kana hannun sojoji ne..." Doctor Hasheem ne ya fusata a tsawace yace "Please Doctor am asking you about my sister..." Girgiza kai Doctor yayi sannan yace "kaga ka firgita ƙanwar takan ko.." Lailah ƙanƙame rigar Doctor Mansur tayi tana kuka tareda surutai tana faɗin "ku temake ni!, ku temake ni!! ku temake ni!!!..." Doctor Mansur ne yake faman rarrashinta yana cewa "kinga kinga Lailah kiyi shuru kiji wani zance..." ya kawo bakinsa saitin kunnenta yana mata busa haɗi da shuuuuuu... lokaci guda tayi shuru tana sauraron Doctor, Dr Mansur nuna Hasheem yayi yana faɗin "Lailah kin gane waye wannan?.." girgiza kai ta soma yi da sauri tana cewa "a'a! a'a!! a'a!!! ban sanshi ba, ni ban taɓa ganinsa ba, kar ku barshi ya tafi dani, banason ganin fuskarsa irin na gwaigwai..." ta ƙarasa maganar tana kifa kanta akan lap ɗin Dr Mansur, ɗagota Dr yayi yace "okay kiyi haƙuri zan koreshi yanzu, ɗago kika shin kinsan wancan?.." ya nuna Oga Junaid wanda ya tsaya yaci bomm hannayensa a goye kan ƙirjinsa idonsa a kanta, Lailah ɗagowa tayi takai idonta kan Junaid, da sauri ta kanne idanuwanta da ƙarfi tana ihu tana faɗin "ku fita mun da wancan dodo, banason ganinsa, Lailah batason ganinsu gaba ɗaya, Lailah zatayi kuka idan ba'a fitar mun dasu baaa, wayyo Allah nahh dodonni...." Dr Mansur ne ya ƙwantar da ita yana rarrashinta ya taso yana ce musu "dan Allah kuyi haƙuri Oga Junaid mu fita mu bata wuri ko zata samu nutsuwa..." haka Dr yasa hannu ya ɗago Dr Hasheem suka yi waje yana kuka yana ƙiran sunan Lailah.. Lailah bayan sun fita shuru tayi da yin kukan tana ƙwance tana fuskantar ceilling idonta a ƙafe ko ƙiftasu bata yi, duk fuska ya kokkoɗe ido sun tuttuje babu alaman ƙwalli, ga sumar kanta a baje duk ta fiffige shi, a halin yanzu Lailah bata san kowa ba sai Dr Mansur shima don koda yaushe yana tareda ita ne shiyasa, tana yawan ganinsa amma bayan shi ko wasu likitocin ne suka yo kanta ta rinƙa yi musu ihu kenam har sai sun fita mata a ɗaki... Haka Dr Mansur yaja su Junaid zuwa office ɗinsa a lokacin ya basu kujeru suka zazzauna shima ya zauna yana fuskantarsu daga baya ya soma yin magana yana cewa "a gaskiya bazan ɓoye muku ba Lailah tana buƙatar temako, ta shiga wani irin halin da itama kanta bata san tana ciki ba, kuma wannan halin da take ciki ba haka kawai ta shige shi ba dole akwai abunda ya faru da ita, kodai an buga mata wani ƙarfe akanta ko kuma an gwara mata kai a jikin wani abu..." ya ƙarasa maganar yana kallon Dr Hasheem, Jinjina kai Dr Hasheem yayi sannan yace "eh tabbas ta buga kanta a ƙasan floor ne.." Dr Mansur yace "saidai idan bugata akayi, saboda idan buguwa tayi ita kaɗai ƙwaƙwalwarta bazai juye har haka ba, a baya mun yanke shawarar kaita asibitin mahaukata ne a ɗorata akan sakatiri amma yanzu na canza shawarata baza'a kaita ba saboda tana buƙatar nutsuwa a yayin da take cikin kaɗaici wanda babu hayaniya a gurin, ta hanyar nan zamu samu nasarar magance matsalar ta, idan kuka fuskanta bata buƙatar hayaniya da takuri..." Junaid ne ya ari bakin Dr yace "idan kuwa aka kaita asibitin mahaukata zata rasa sukunin ta ne..." Dr Mansur yace "tabbas hakane.." Dr Hasheem kai a sunkuye yace "yanzu to Dr meka tsara akan wannan al'amarin?..." Dr Mansur yace "Ni a yanda na tsara Lailah zata cigaba da zama a wannan asibitin, insha Allahu zan bata duk wani kulawar da take buƙata, zan san yanda zanyi na magance matsalar ta Insha Allahu..." Dr Hasheem murmusawa yayi yana zubda ƙwallah yace "Nagode sosai Dr.." hannu yakai yana goge hawayen fuskarsa yana shirin miƙewa tsaye, Dr Mansur yace "amma Dr Hasheem yakamata kaima ka tsaya a duba lafiyar jikinka ko? naga kaji raunuka sosai a jikinka..." Dr Hasheem komowa yayi ya zauna yana faɗin "Ok thanks" Miƙewa Junaid yayi yana cewa "toh Ni zan wuce.." Dr Mansur ne shima ya miƙe tsaye yana bashi hannu sukayi sallama, Junaid hannu yasa cikin pocket ɗinsa ya zaro damin kuɗi dollars dollars sun kai guda ɗari biyar ya miƙawa Dr Hasheem yana faɗin "ga wannan zaiyi maka amfani waran jinyar ƙanwarka..." Dr Hasheem juyar da kai yake tsabar takaici kamar zai haɗiyi ransa, ba mutumin da yafi tsana a yanzu kamar Junaid, hannu yasa yana goge hawayen da yake zubo masa cikin ɓacin rai ya miƙe tsaye yana fuskantar Junaid yace "a'ah ka riƙe kuɗin ka bana buƙatarsu domin nima inada fiye da waɗannan..." ya kuma haɗe hannayensa biyu tareda durƙusawa ƙasi yana roƙan Junaid yace "dan Allah! dan darajar Manzon Allah Sallallahu alaihi Wasallama ka fita daga cikin rayuwar mu, bama buƙatarka a cikin rayuwar mu, ni na rantse da rabbani waran da kake ma bazan biyo hanyar ba balle mu haɗu, duk abunda ya shafeka kuma na barshi har abada, asibitin mahaifiyarka yanda iyayena suka bar duniya haka nima na daina aiki acikin asibitin na, dan Allah Junaid ko a hanya ka gan mu kada ka nuna ka san mu ma dan Allah 🙏🙏..." Junaid kawar da kansa gefe yayi yana murmushi shi abun ma dariya yaso bashi, hannu yasa ya ɗago Dr Hasheem tsaye yana faɗin "okay don't worry dat is your concern, I'll do my own business..." yana buga kafaɗarsa a hankali ya kuma cewa "quick recovery..." yana kaiwa nan ya juya yayi ficewarsa, "kai ɗin Dr Hasheem meya haɗa ka da Junaid kuma, naga ku ɗin abokai ne kuma ma naji kana cewa kabar aiki a asibitin su shin kasan a yanda zaka samu aiki yanzu kuwa?...." a cewar Dr Mansur wanda idonsa ke kan Dr Hasheem.. Ajiyar zuciya Dr Hasheem ya sake tareda faɗin "Allah ya wadaran irin wannan Abokantaka, abokin da bazai iya rufa maka asiri ba ai ba aboki bane, abokin da burinsa yaga ya ƙuntata maka ai ba aboki bane, abokin gaskiya bazai so a taɓa tsokar jikin ɗan uwansa ba da sunan duka amma yau gashi Junaid abunda yasa aka aikata mun, yanzu yabar aboki ya koma babban maƙiyi na..." ya ƙarasa maganar yana huci.. Dr Mansur girgiza kai kawai yayi yace "Allah dai ya sawwaƙe..." ya furta hakan tareda miƙa masa takardar maganunnuwan da zai siyo.. karɓa Dr Hasheem yayi tareda zabura da sauri ya miƙe yana tafiya daƙer yana jan ƙafa kamar wani gurgu da haka ya fice... Dr Mansur kallonsa yake har ya fice kawar da kai yayi yana murmushi, (kuna ji ana cewa Dr Mansur toh ba tsoho bane, haɗaɗɗen saurayi ne fari kyakkyawa mai yawan murmushi, wanda kuɗaɗe suka ratsa shi, mahaifinsa asalin maloniya ne ya sanu a ko ina, wannan asibitin kuma mallakin Dr Mansur ne wanda dawowarsa daga ƙasar Egypt ya kammala karatun master's ɗinsa a bangaren likitanci hakan yasa ya buɗe babban hospital ɗinsa wato *IHSANN GENERAL HOSPITAL ABACHA ROAD ABUJA*..) ***** ________ Bayan fitar Junaid daga hospital cikin gari ya nufa yana yawon nuna photon Ayush ko akwai wanda yasan a yanda take, amma har yanzu shuru babu amon labarinta, miƙar hanyar express road yayi wanda yake tsakanin Abuja to Kaduna tafiya yake a hankali da motarsa yana kallace-kallace ko zaiga Ayush, har ya soma barin cikin garin, kana ganinsa kasan akwai damuwa ƙarara a saman fuskarsa yana tafe yana maganar zuci "Allah Ubangiji ka haɗani da wannan baiwar takan, aina zan ganki Yushert?..." tafiya yayi mai nisan gaske har yabar cikin garin Abuja sosai, parker motarsa yayi a gefe guda sannan ya fito ya tsaya a jikin motarsa yana kallece-kallece, acikin daji yake tsugugu domin ba alamar motsin mutane, ba kuma gida ko ɗaya sai kukan tsuntsaye ga kuma wani irin zugugun sanyi da akeyi, lokaci guda Junaid ya ƙanƙame jikinsa da hannayensa tsabar sanyin da yake ratsa shi, ba shiri ya shiga cikin motarsa ya ɗauko rigar sanyi da face mark ya sanya su tareda ɗaukar torch light ya saka a aljihunsa sannan ya shiga cikin dajin, tafiya yake ba ƙaƙƙautawa har saida duhu ya soma shiga, ya haɗu da macizai sunfi a ƙirga amma saidai ya wuce su yana ƙwalla ƙiran sunan Yushert, tazararsa da bakin ƙwalta tafiya ne mai nisan gaske a yayin da duhu ya biyo baya, domin ko gabansa baya iya gani kunna hasken torchinsa yayi ya cigaba da tafiya yana haske-haske duk yabi ya gaji, jikinsa har ciwo yake, ganin bazai iya cigaba da tafiyar ba ya tsaya a guri ɗaya ya haɗe hannayensa biyu a saitin bakinsa ya soma ƙwallah ƙiran Ayush a cikin dajin nan, "Yushertttt! Yushertttt!! Yushertttt!!!..." yana cikin ihun ƙiranta ne yaji ta bayansa ance "Yaya Junaid..." da sauri Junaid ya waiwaya da murmushi a fuskarsa yana haska wacce ta ƙira sunansa, ganin Ayush yayi a tsaye tana sanye da doguwar riga kayinta ba mayafi, itama tana tsaye sai faman murmushi take, da saurinsa ya nufi gurin da take yana faɗin "my Yushert Ina kika shiga ne inata nemanki, kin wahalar dani sosai..." yakai hannu zai rungumeta gani yayi ta ɓace ɓattttt! a firgice yayi baya ya faɗi ƙasi a zaune sai faman zazzaro ido yake jikinsa na kakkarwa, a ruɗe yake lalumar yanda torchinsa yake a yashe, cikin sa'a ya sameta yana ƙoƙarin tashi tsaye saiji yayi dajin ya soma ɗaukar dirin dariya, dariya akeyi ta ko ina, cikin ƙatuwar murya da kuma siririyar murya nan take muryoyi da yawa aka fara ƙiran sunan "Yushertttt! Yushertttt!! Yushertttt!!! Yushertttt!!!!" ana kokkoyan sunan da Junaid yake ƙira! Junaid gaba ɗaya ya ruɗe wani irin haɗiyar yawu yayi duk ya haɗa gumi still muryar mutane yake ji ta saman bishiyoyin jejin, Miƙewa yayi a razane ya soma cin uban gudu ko waiwaye baya yi, gudu yake sosai har saida ya daina jin dariyar mutanen daiden lokacin yayi tuntuɓe ya faɗi ƙasi, ɗagowar da zaiyi ƙwatsam sai yaga wata mata sai birgima take a ƙasi tanata ihu da tsohon cikinta, haskata yayi a ruɗe yace "Yushert?..." ita kuwa Ayush kuka take tana ƙiran sunan Junaid "dan Allah Yaya Junaid ka temake ni, wayyo cikina ciwo zan mutu wayyo Allah nahhhh..." da rarrafe yazo ya ƙaraso gurinta yana faɗin "Yushert! Yushert ki ƙwantar da hankalinki gani nazo gareki kinji koh, ki daina kuka..." Ita kuwa cewa take "wayyo Yaya Junaid haihuwa zanyi ka danna mun cikina, raɗaɗin nake ji haihuwa zanyi, bazan iya motsawa baaa..." Junaid hannu ya ɗora akan cikinta yana matsawa a hankali ga torch kuma a gefe yanda ya ajiye shi, yana cewa "zaki haihu yanzu ki kwantar da hankalinki, da ɗan mu zamu koma gida cikin ƙwanciyar hankali..." Ayush tana nishi a hankali tace "yauwa Yaya Junaid yaro na ɗaya ya fito, cigaba da matsa mun cikin wayyo yaro na biyu ya fito, ahhhh yaro na uku ya fito, i love You Yaya Junaid ashhh yaro na huɗu ya fito, yauwa! yauwa!! cigaba ahhh yaro na biyar ya fitoo..." Junaid zaro ido yayi waje ganin jarirai har guda biyar yace "Yushert har yara nawa zaki haifo mana ne?..." Ayush tana murmusawa a hankali tace "yara Ashirin ma sun isa..." a wahalce Junaid ya aɗiyi yawu yace "Yushert yara Ashirin sunyi yawa ai...." kafin ya ƙarasa maganar yaji tace "yauwaaa yara biyar sun fito a jere, mammatsa mun cikin sosai yauwa yara biyu sun fito suma a jere, ahhssh ahhhh wayyo sauran kaɗan sauran yara takwas su fito..." Junaid gaba ɗaya baya cikin hayyacinsa kawai matsa mata ciki yake lokaci guda kuwa tayi wani irin yunƙuri saiga sauran jarirai takwas sun wantsilo, ajiyar zuciya tayi sannan tace yauwa Masha Allah sun gama fito wa, yanzu zamu iya tafiya gida ko?.." Junaid a tsorace yake ja da baya ganin yanda jariran nan suke miƙewa tsaye ƴan ƙananu dasu sai manya-manyan kayuwa, kayin jariri ɗaya yayi biyar ɗin kayin Junaid, duk ɗinsu haka suka tashi su ashirin suka nufo gurin Junaid suna kuka suna faɗin "Babaa! Babaaa!! Babaaa!!! Baban muuu!!!!..." Junaid ja da baya yake sosai sai faman hashaska su yake, a firgice ya kalli yanda Ayush take a ƙwance yaga ta washe baki har zuwa kunne tana masa dariya ga babu haƙwarai a bakin sunyi ɓaɓurka. Da gudun gaske Junaid ya miƙe ya fara gudu kamar zai fura sama haka yake wannan gudun ceton rai, torchin ma bai san lokacin da ya jefar shi ba, yana zuwa saitin wani bishiya kawai ya kama yahau kan bishiyar nan, saida yaje kusan ƙarshen bishiyar tukun ya tsaya yana fitar da numfashi daƙer, yana ganin kamar ya tsere daga hannun jariran nan, haka ya ƙwantar da kayinsa kan bishiyar ya lumshe ido yana haki can yaji kamar ana taɓa shi da sauri ya buɗe idonsa yana buɗewa yaga wannan matar mai haihuwar nan ne a gabansa akan bishiyar, idanuwanta sun koma green ga yanda take wani irin dariya bakinta har kan kunnenta, ga babu haƙori ko ɗaya a bakin, bakinta kuwa duk jini a firgice Junaid yayi wani irin ihu a razane ya zamo daga kan bishiyar ya faɗo ƙasi, kansa ne ya bugu da wani dutsi nan take ya sume a wajen..... ****** A can headquarters kuma sunata ƙiran wayan Junaid akan a sanar masa cewar wani mutumi yazo ya sanar cewar shi da kansa yakai Ayush har jejin da take da mashin ɗinsa, amma basu samu wayarsa ba, wayar tana ringing amma ba'a picking dake a cikin motarsa yabar wayar, Malam Lawan shima yakai sau nawa yana ƙiran wayansa amma ba'a picking har zuwa washe gari Sojojin headquartersu suka yi tracking wayarsa suka gano a yanda yake, abun ya basu mamaki ganin a dajin da akace Ayush take anan shima yake, anan suka fara shiri zasu je cikin wannan dajin, sojoji guda biyar aka ware waɗanda zasu je kuma acikin elekwabta zasu tafi saboda mota bazata shiga dajin ba, Around 10:00AM Junaid yana ƙwance a cikin daji tin cikin dare har zuwa yanzu bai farfaɗo ba, ga hadari yanda ya haɗu sai walƙiya ake lokaci guda aka fara ruwan sama, wannan ruwan da yake sauƙa masa ne yasa ya tashi a firgice yana ambaton sunan "Yusherttt...." waige-waige yake ganin shi kaɗai a cikin daji yasa ya miƙe yana tangal-tangal kamar zai faɗi haka yake tafiya hajijiya na ɗibarsa ga kuma ruwan sama yanda yake jibgarsa, daiden lokacin saiga elekwabta na sojoji yanata yawo a sama, suna neman yanda zasu ga Junaid da Ayush! sunyi nasarar ganin Junaid sakamakon ɗaga musu hannu da yake yi, a hankali elekwabta ta sauƙo duk suka fito da bindigu a hannunsa suka zo gurin da yake suna faɗin "Ogah Junaid are you okay?..." wani irin matsanancin ciwon kai ne yake damunsa ga yunwan da yake ji da ƙishin ruwa haka suka rirriƙe shi suka saka shi a cikin jirgin, su kuma suka bazu neman Ayush acikin wannan ruwan ...... *TOH PAH 🤣 KU KUKE GANIN MU BA MU KE GANINKU BAA🤣🤣🤣* *AUNTY HABIBA, AUNTY KHADIJA, AUNTY HAJJAJO NACE BAAA HOW MARKET🤪🤪* *WANNAN PAGE ƊIN NA ALJANU NE BA NAMU BANE🤣🤣🤣🤣* 𝑡𝑦𝑝𝑖𝑛𝑔✍️ 𝗠𝗔𝗧𝗔𝗥 𝗗𝗔𝗠𝗨𝗦𝗔 the wife of a tiger🐅🐅🐅🐅 𝙼𝚊𝚕𝚕𝚊𝚔𝚒𝚗 𝙰𝚜𝚖𝚎𝚎𝚝𝚊𝚑 ✍️✍️ 𝙿𝚊𝚒𝚍 𝚋𝚘𝚘𝚔 𝚌𝚊𝚕𝚕 𝚘𝚛 𝚠𝚑𝚊𝚝𝚜𝙰𝚙𝚙 09065443871 *💫💫{{N W A}}💫💫* Book two C̶h̶a̶p̶t̶e̶r̶ 51 ➡️ 52 _________________ Doctor Hasheem ƙwance yake akan sofa ya ɗora hannunsa ɗaya akan goshi yana fuskantar ceilling ido a rufe sai shan bacci yake a nutsu, baccin wahala, yana cikin baccin yaji anata buga ƙofar falo dake shima a falon yake a razane ya farka yana addu'a, bugu ake bana wasa ba haɗe rai yayi fuska a murtuƙe ga yayi wani irin muni bugu da ƙari ma sumar kansa da aka aske, sai fama tsuka yake tayi ya miƙe daƙer yana ɗingishi yayi bakin ƙofa yana faɗin "wai waye ne kam dallah.." ya ƙarasa maganar daiden lokacin ya buɗe ƙofar ƙirjinsa ne yayi wani irin bugawa da ƙarfin gaske ganin Police waran su biyar sunyi cirko-cirko suna kallonsa, a kiɗime Dr Hasheem ya fara ƙinƙina yana faɗin "la la lafiya kuwa na ganku?..." ɗaya daga ciki ne yace "inda lafiya ne ai bazaka ganmu a gidanka ba..." Dr Hasheem buɗe baki yayi yana shirin yin magana ƙwatsam idonsa ya sauƙa akan Daddy wato mahaifin Maimoon, juyawa yayi da gudu zai koma ciki ƴan sandan sukayi saurin riƙo shi suna cewa "Oh guduwa wai zakayi?.." rantse² ya fara yi yana magiya haɗe da cewa "dan Allah ku temaka mun wallahi jiya na fito daga hannun sojoji, kuyi mun rai da Allah..." Baban Maimoon ne yazo gabansa ya tsaya yana huci shi alokacin bai ƙi yasa bindiga ya harbe kan Dr Hasheem bama, wani irin kallo ya watsa masa sannan yace "kai Kanada bakin magana ne Hasheem? shin ka tuno da yarinyar da kayiwa fyaɗe? wallahi kaban mamaki matuƙa, nayi tunanin kai mutumin kirki ne har na yarda dakai na baka amanar ƴata ashe kai ba ɗan goyo bane, kai butulu ne fool like you! wallahi albasa bata yo halin ruwa ba, mahaifinka mutumin kirki mai dattaku inda ace yana raye kayiwa ƴata fyaɗe toh wallahi babu abunda zai hana ya yageka daga cikin ƴaƴan daya haifa..." Dr Hasheem kuka yake sosai ya haɗe hannayensa biyu yana roƙon baban Maimoon "dan Allah Daddy kayi haƙuri ka yafe mun, nayi kuskure babba nasan ban kyautawa Maimoon ba, amma wallahi har cikin zuciyata banyi niyar aikata mata haka ba saboda Maimoon macece mai mutunci kuma ta fito a gidan mutuntaka, har yau har gobe inason Maimoon, Ni ba mutumin banza bane saboda bana harkar mata, bana zuwa gidan club bana shaye-shaye kuma Ni ba ɓarawo bane...." kafin ya ƙarasa iddasa maganarsa Daddy yayi saurin darara masa wani irin gigitaccen tsawa tareda cewa "sai dai kai butulu ne, banason jin komai daga bakinka Hasheem domin kana ƙara hura mun wuta ne acikin zuciyata, ji nake kamar na murɗe maka wuya a yanzun nan, amma ba komai yau zakayi ƙwanan bayan kanta zuwa monday zamu shiga kotu daga nan za'a yanke maka hukuncin zaman gidan yari na tsawon shekara 25, hukuncin fyaɗe kenam, na barka lafiya..." yana gamawa da Hasheem ya maida kallonsa kan ƴan sandan gurin yana ce musu "kuje dashi kuyi ta dukansa har saiya fita hayyacinsa kafin ranar da za'a shiga kotu, a tura shi prisoner yaje ya ɗanɗani kalar abincinsu har ya tsufa ya sheƙe...." cikin ɓacin rai ya ƙarasa maganar tareda wucewa a fusace yayi tafiyarsa, yana jin yanda Dr Hasheem yake roƙonsa da yi masa magiya amma ko sauraronsa baiyi ba, Haka ƴan sandan nan suke jansa suna ƙwaɗa masa sandunan hannayensu, fashewa yayi da matsanancin kuka yana mai ƙara jinjina kansa a halinda ya tsinci kansa... ****** Junaid yana zaune acikin elekwabta yana dafe da goshinsa tunowa yake da abubuwanda suka faru dashi a daren jiya gaba ɗaya ya rasa sukunin sa, ga idanuwa sunyi lufu-lufu, yana cikin wannan halin yaji ihun Ayush ya daki dodon kunnensa da ƙarfin gaske, a kiɗime ya ɗago yana waige-waige, ihu na biyu ya sake ji a gigice ya sauƙo daga kan elekwabta da gudun gaske yake bin yanda yake jin ihun ga kuma ƙarar harbin bindiga da yake ji, ji yayi kamar furawa yake tsabar gudun da yake tiƙa yana haɗawa da tsalle, yana isowa wajen ya daina jin ihun sai harbi da yake ji, haka yake ratsa jeji yana kutsawa ciki ko waiwaye baya yi haka yake tiƙan gudu, itama Ayush sai faman gudu take tana waiwaye, jin ta bugu da abu ne yasa tayi saurin kallon gabanta ƙara tasau tayi baya sauran kaɗan ta faɗi yayi saurin riƙo hannunta ya jawota jikinsa suna maida numfashi a tare, da sauri yakai hannunsa biyu ya tallafo fuskarta suna kallon juna Junaid yana haki yace "Yushert ki ƙwantar da hankalinki ba abunda zai sameki..." tana kuka cike tsoro da firgici ta ƙanƙame hannun Junaid tana faɗin "Yaya Junaid zasu kashe ni ne, na gansu da bindigu suna harbawa wallahi kasheni zasu yi..." tana maida numfashi sama² tareda waige-waige ko sun biyota, kafin kace me sojojin har sun iso yanda suke a tsaye duk sun kewaye su sun saita bindigunsu, ɗaya daga cikine yace "Ogah Junaid ka miƙo mana ita nan, saboda ance mana duk rintsi duk wuya mu tafi da ita..." Ogah Junaid yana rungume da Ayush yace "ku jeku zan kai muku ita da kaina.." suka ce "Please Ogah Junaid muna bin tsarin aiki ne, umarni ne daga shuwagabannin mu, idan kuma taƙi zamu harbeta ne..." Ayush jin haka ta ƙara ƙanƙame Junaid jikinta na ɓari da ƙarfi tana kuka tace "dan Allah Yaya Junaid kada ka bari su tafi dani wallahi kasheni zasuyi.." ga tumbi kuwa ya fito sosai, Girgiza kai Junaid yayi sannan ya ƙira sunan ɗaya daga cikin sojojin su murya a sanyaye yace "Commander inaso kamun wata alfurma please, ku bar mun ita a yanzu nace idan ta samu nutsuwa zan kai ta har quarters ɗin..." ya kalli sergeant yace "kuyi haƙuri nasan umarni ne daga sama amma kuyi mata uzuri saboda abunda ke cikinta, idan kun koma ku sanar cewa tana gurina amma nayi alƙawarin gobe zan kaita da hannuna pleasee my Man's...." ya marairaice yana musu magiya... Sauƙar da bindigunsu sukayi suka ce "shikenam taci albarkacinka da kuma cikin dake jikinta amma badan haka ba babu abunda zai hana mu harbe mata ƙafa sannan mu kaita tinda ita tanada ƙafar guduwa...." Jinjina kai Junaid yayi yana cewa "ok toh kuje ku zan isoku, motata tana bakin hanya..." Commander yace "but ka cika alƙawari fa gobe ka kaita headquarter saboda kasan halin General, ga kuma marshal shima ya hura wuta a kai..." Junaid kaɗa musu kai kawai yayi yana rungume da Ayush, Sergeant yace "ok Ogah Junaid muje mu hau elekwabta sai mu sauƙe ka a bakin hanya ka shiga motarka, kasan akwai tazara mai nisan gaske daga nan zuwa bakin road..." Junaid ya amsa tayinsu yayi wa Ayush ɗaukar luɗa suka fara tafiya a cikin dajin nan, akwai ɗan nisa kaɗan kafin su je gurin da elekwabtarsu take... Shi Junaid yana lallamin sojojin ne ba wai don yana jin tsoronsu bane sai don yasan suma bayin kansu bane, umarni aka basu daga wajen shuwagabanninsu gaba ɗaya shiyasa ya shugo da magiya a ciki saboda ya tseratar da Ayush.... Elekwabta suka shiga gaba ɗayansu still Junaid yana rungume da Ayush kamar wanda za'a ƙwaceta da ƙarfi, suna zuwa bakin hanya aka sauƙe su! su kuma sojojin suka yi gaba abinsu acikin elekwabta, Junaid a seat back ya ƙwantar da Ayush yana faɗin "kwanta ki huta..." shima ya zagayo ya shiga ya fara tuƙin motar a hankali daga baya ya soma gudu da motar kamar zai tashi sama, Allah² yake su shiga cikin gari domin ba ƙaramin wahala yasha ba, duk jikinsa sai ciwo yake masa ga wani matsanancin yunwa da yake ji, tin jiya da safe rabonsa da abinci... Around 2:30pm Junaid suka iso gida a wahalce, parking yayi a wajen space parker ya fito da saurinsa ya zagayo ya buɗe Ayush, hannu yasa ya kikkimeta suka nufi cikin babban falon da zai sadasu da ƙananun ɗakunansu na ƙwanciya, kai tsaye upstairs ya haura, yana zuwa ƙarshen stair ya sake shan ƙwana ya ƙara haura stairs na biyu, yana kaiwa ƙarshen nan ya kuma haura na uku ana ukun ne ɗakinsa da ƙafarsa ya tura ƙofar da ƙarfi ta buɗu, yana shiga ya zaunar da Ayush a bakin gado, gaba ɗaya duk ta rarrame ta fita hayyacinta, har tayi duhu kaɗan ga rigar jikinta tin data tafi bata canza ba saboda iya shi kaɗai take da duk yayi datti yayi baƙi ƙirin, sumar kanta shima ya cakurkuɗe babu gyara duk yayi ƙura da datti, haƙwaranta har sun canza kolo saboda datti, ita kanta rabon da tayi wanka tin data bar hospital gurin Junaid, sai hamami take tayi. idanu sunyi lufu-lufu sun shanye kamar wacce tayi maye haka take bin Junaid da kallo, shima durƙusawa yayi a gabanta ya ɗora hannayensa biyu saman cinyarta haɗe da riƙo hannayenta yana murzasu, cikin takaici yake kallonta fuska ba Annuri daƙer ya iya cewa "Yushert shin abunda kikayi kin kyauta mun kenam? shin kinyi wa kanki adalci? dubi yanda kika koma fa kamar wata marar gata, kin cutar dani sosai kin ƙuntata mun matuƙa sannan kin wahalar mun da yarona wanda baiji ba bai gani ba why Yushert?...." kuka ne ya kuɓuce mata tana ture hannayensa daga cikin nata tareda faɗin "Ni ka ƙyaleni! rayuwata a cikin dajin tafi mun komai daɗi, bana son kasancewa da kowa guri ɗaya..." Girgiza kai Junaid yayi sannan yace "amma kina sane da igiyar Aurena akan ki?..." ƙura masa ido tayi tace "daman tsawon watannin nan baka sakeni ba?.." cije leɓɓensa yayi yana kallonta yace "meyasa zan sake ki? alhalin keɗin rayuwata ce" katse shi tayi da cewa "duk da kashe maka mahaifiya dana yi?..." rufe idonsa yayi sosai yana cije lips ɗinsa wani irin tafasa zuciyarsa take yi kamar wanda ake hura masa wuta a ciki ya danne yayi ƙarfin halin cewa "please Yushert ki bar mun wannan maganar, mahaifina ya mutu ata sanadiyar iyayenki, mahaifiyarki ta mutu ata sanadiyata, haka kuma mahaifiyata ta mutu ata sanadiyar ki, shin acikin mu wa akafi cuta? Yushert inaso ki sani cewa ƙaddara bata taɓa tsallake bawa, yakamata mu rungumi ƙaddarar mu muyi haƙuri mu zauna...." bai kai da ƙasara maganar ba ta katse shi da cewar "saboda baka kishin mahaifiyarka? nifa da hannuna na kasheta har lahira..." zabga mata wani irin gigitaccen mari yayi saida ta kife akan gadon, ɗagowa tayi tana kuka tace "Ni ka sakeni, na haramtawa kaina zaman Aure, bazanyi rayuwar Aure da kowa ba, nifa ƴar ta'addace da hannayena nayi kisan kai...." ta ƙarasa maganar tana fashewa da matsanancin kuka harda majinar ta, ta miƙe tsaye tana ƙoƙarin guduwa ya riƙota yana cewa "Yushert ki saurareni, idan kika fita yanzu kasheki zasuyi..." ita kuwa ƙoƙarin ƙwacewa take tana faɗin "Ni ka sakeni nafi son su kasheni daman na gaji da zaman duniya, ka sakeni ko na kashe kaina, wallahi zan kashe kaina, zan kashe kaina idan baka sakeni baaaa....". tana kuka tana maganganu marasa lissafi ganin taƙi dawowa hayyacinta ne yasa ya kuma zabgeta da mari a ruɗe ta hautsina saman gado ta kifu da cikinta, dafe cikinta tayi tana kuka haɗi da cewa "wayyo Allah nah cikinaaaa..." a tsorace Junaid yayo kanta yana ƙiran sunanta a kiɗime "Yu Yu yuu yuushertt kina lafiya ko? Please am sorry, so so srrrry my Yushert...." ganin yanda take juyi tana riƙe da ciki ga kuka yaƙi tsayawa yace "Yushert kina so ki kasheni ne?..." wani irin ƙara yayi ya dafe saitin zuciyarsa ya dungura shima akan gado tareda ɗauke numfashinsa ido a rufe, Ayush jin Junaid yayi ƙara kuma ba motsi yasa tayi saurin ɗagowa ta nufi yanda yake da rarrafe akan gadon tana ƙiran sunansa da ƙarfi cikin tashin hankali "Yayaaa Junaid! Yaya Junaidd!! wayyo Allah Yaya Junaid karka mutu ka barni dan Allah, dan girman Allah Yaya Junaid ɗina ka tashiiiiii wallahi inasonka, ina ƙaunarkaaa zan zauna dakai a matsayin matarkaaa...." sake fashewa tayi da kuka tana jijjigansa da ƙarfi, kamar ranta zai fita haka take faman ƙiran sunansa cikin kuka, kifar da kanta tayi a saman ƙirjinsa ta rungumeshi sosai tana faɗin " shikenam tinda ka mutu nima rayuwata bata da wani amfani, gwara nasha poison nima na mutu inyaso azo a kwashi gawar mu a tare..." ta tashi cikin ƙarfin hali har cikin zuciyarta ta ƙudurta hakan, tana kuka taji an riƙe mata hannu da sauri ta kalli hannunta taga Junaid ne ya riƙe mata hannu sai faman tintsirewa yake da dariya yana kallonta, haushi ne ya isheta cikin ɓacin rai tace "daman wasa kake yi Yaya Junaid?..." ganin yanda yake mata dariya yasa takai hannu tana kai masa duka da hannu bibbiyu tana kuka daga ƙarshe ta rufu akansa tasa hannu ta rungume shi sosai tana kuka tareda faɗin "inasonka sosai Yaya Junaid, ka gafarce ni nima ba'a son raina na tafi na barka ba, inason kasancewa a tare dakai, duk da nasan yanzu hukuma nemana suke..." ta sake fashewa da kuka.. Junaid hannayensa biyu ya zagayo dasu ta bayanta ya rungumeta shima bakinsa a saitin kunnenta yake mata magana a hankali ta sigar rarrashi, daga baya tayi shuru tana jin yanda yake ɗan bubbugan bayanta a hankali, saida sukayi kusan awa guda a haka tukun Junaid ya mirgino da ita ya ƙwantar ta idonsa cikin nata yace "wait for me bari naje na haɗa miki ruwan wanka koh..." ya ƙarasa maganar tareda yi mata sigina.... tashi yayi ya shiga cikin toilet can ya fito yazo ya ɗauki Ayush suka shiga ciki tare, yayi mata wanka sosai da ruwa kala uku kuma ko wanne ruwa da kalar ƙamshin turarensa, haka ya wanke mata kayinta tass ya koma asalin yanda yake baƙi ƙirin sai sheƙi yake yana ɗaukar ido, yayi mata shevin gashin hammatar ta sannan shi da kansa yayi mata sheving farjinta, saida ya gama mata wanka tukun shima ya cire yayi wankansa cikin nutsuwa da kwanciyar hankali, a yayin da yake wanka ita kuma Ayush tana gefe tana brush.... A tare suka fito yana sanye da gajeren wando mai kama da pant, bayan shi babu komai a jikinsa ya fito yana ɗauke da Ayush a hannunsa wanda ita kuma towel ne a ɗaure saman ƙirjinta, ajiyeta yayi a bakin gado ya ɗauko creams kala² dana gyaran gashi duk ya mulmulka mata, yayi mata ƙwalliya sannan ya gyara mata gashin kanta yayi rolling da gashin saboda tsayin yayi yawa, ya feffesheta da turaruka kala² masu ƙamshin gaske, saida ya kammala shiryata tsab sannan ya nufi wardrobe ya ciro wata farar jallabiya na mata a cikin akwatinta da sauran ƙananun abubuwanta yazo ya sanya mata su ya ɗauki Hirami mai zanen fari da baƙi ya naɗa mata a kanta ya fitar mata da tsolon gashinta ta waje, ya kuma ƙara fesheta da turare, ɗakin duk ya kaure da ƙamshin turaruka kala-kala, a gaskiya Ayush ba ƙaramin kyau tayi ba, kamar wata kyakkyawar balarabiya ƴar ƙasar madina, Junaid tsayawa yayi yana kallonta kamar ba Yushert ɗinsa ba, sai faman murmushi yake baki yaƙi rufuwa, daga baya shima ya shirya cikin wata danƙararriyar gizna water fruit, yasha hula kalar gizna takalmi jinin sarauta kalar gizna shima ba ƙaramin kyau Oga Junaid yayi ba, Ayush sake baki tayi tana kallonsa ita tinda take da Junaid bata taɓa ganin shi acikin manyan kaya irin haka ba, saiya fito a mazannin Alhaji Junaid, rufe bakinta tayi da hannunta tana dariya, shima tsayawa yayi yana kallonta yace "Ni kike wa dariya ko..." tace "daman kanada shaddodi da giznoni ne?..." Murmushi yayi har saida dimple ɗinsa ya lotsa sosai ga saje baƙi ƙirin a kwance saman fuskarsa zuwa gemunsa ba ƙaramin haɗuwa yayi ba yace "ke nifa yanzu na zama Baba dole na riñƙa shiga cikin manyan kaya yanzu, amma ba kullum ba domin har na fara takura wallahi, jikina yayi mun nauyi ni cire kayan zanyi ma..." ya ƙarasa maganar tareda sa hannu zai cire rigar Ayush tayi saurin zuwa gabansa tana riƙe da hannunsa tace "a'ah dan Allah mijina kayi kyau sosai kar ka cire..." dariya yayi tareda riƙe ƙugunta yace "toh shikenam matata na bari, yanzu jirani bari naje na nemo mana abunda zamu ci koh?..." kaɗa masa kai tayi cikin shagwaɓa tace "ehhh Baby na jin hungry..." hannu yakai yana jan dogon hancinta cikin wasa yace "haka itama mommin Baby na jin hungry..." yana kokkoyan yanda tayi shagwaɓa, cikin jin kunya takai masa naushi kan ƙirjinsa a hankali tace "uhmm uh uhmmm nasan Daddin Baby shima na jin hungry..." duk ɗinsu suka tintsire da dariya cikin zolayan juna suka rabu shi Junaid yayi waje zaije restaurant domin nema musu abunda zasu ci, Ita kuma ƙwanciya tayi akan gado tana shaƙar A.C cikin ɗakin da murmushi saman fuskarta da haka bacci ɓarawo yayi awun gaba da ita.... A ɓangaren Doctor Hasheem kuwa yana ƙwance a bayan kanta sunyi masa jinajina har gagara tashi yayi, yana ƙwance ido a lumshe sai fitar da numfashi yake a hankali, domin ba ƙaramin wahala yake sha ba, wannan karan kam tsabar duka jini har ta hancinsa yake fita, ga sun cire masa haƙori ɗaya ta gefe, jibi kuma za'a shiga kotu..... 𝑡𝑦𝑝𝑖𝑛𝑔✍️ 𝗠𝗔𝗧𝗔𝗥 𝗗𝗔𝗠𝗨𝗦𝗔 the wife of a tiger🐅🐅🐅🐅 𝙼𝚊𝚕𝚕𝚊𝚔𝚒𝚗 𝙰𝚜𝚖𝚎𝚎𝚝𝚊𝚑 ✍️✍️ 𝙿𝚊𝚒𝚍 𝚋𝚘𝚘𝚔 𝚌𝚊𝚕𝚕 𝚘𝚛 𝚠𝚑𝚊𝚝𝚜𝙰𝚙𝚙 09065443871 *💫💫{{N W A}}💫💫* Book two C̶h̶a̶p̶t̶e̶r̶ 53 ➡️ 54 Bayan kwana biyar da yankewa Dr Hasheem hukuncin zaman gidan prison na tsawon shekara 25 akan yiwa yarinya fyaɗe... a ranar da aka kai Dr Hasheem prison a ranar Maimoon ta santalo kyakkyawan yaronta, amma saidai mahaifinta yayi fushi da ita ko amsa sallamarta bayayi da zarar tazo yanda yake, haka idan ta gaishe shi baya amsa mata, amma saidai yayi halacci ɗaya daya siyo ƙaton rago yace a yankawa jariri sanna kuma shi ya bada umarni a sanyawa jariri sunan mahaifin Dr Hasheem wato Abubakar, Maimoon taji daɗin haka sosai saboda ko ba komai ya nuna yana son yaronta, Maimoon ta saka wa yaron sunan inkiya wato "Rapeekh", saidai ba'ayi wani hidimar suna ba... yayin da shi kuma Dr Hasheem yana can cikin mawuyancin hali shi kaɗai kamar wani marar gata haka yake zaune yayi tagumi yanata nazarin abubuwa, gaba ɗaya duk ya rarrame ya fita hayyacinsa, suturar dake jikinsa irin na ƴan cikin prison ne kowa an rubuta masa number a bayan rigarsa... ****** Shi kuma Junaid ya kulle kansu a cikin gida saboda sojojin da suke yo masa zirga-zirga akan ya bada Ayush su tafi da ita amma sam yaƙi, yanzu baya fita aiki saboda wannan matsalar, koda yaushe suna cikin ɗaki a manne da juna yauma kamar kullum suna ƙwance akan gado a yayin da ita kuma Ayush take kwance saman ƙirjinsa, tace "Yayana.." ya amsa mata da "na'am ƙanwata ya akai?.." ɗagowa tayi ta zauna tana fuskantarsa tace "meyasa ka kasa cika alƙawari?.." shima idonsa akanta yana cije leɓɓen sa yace "Alƙawarin mai?.." ɗan turo baki tayi a shagwaɓe tace "ka ɗaukarwa sojojinku Alƙawarin zaka kaini gurinsu da hannunka yanzu kuma yau kusan sati guda suna binka amma kaƙi sauraronsu ka kashe wayanka gaba ɗaya, ai baka kyauta musu ba koh kuma zasu ɗauke ka maƙaryaci marar cika alƙawari kuma suna ganin girmanka..". ajiyar zuciya Junaid ya sauƙe yana lumshe ido yace "Yushert a halin yanzu bana ƙaunar rabuwa dake, bansan wani hukunci zasu yanke miki ba, bazan iya barinki ina ji ina kallo su hukunta ki ba..." Ayush katse shi tayi da cewa "amma baka ganin abunda kayi zai iya shafar aikinka?..." yana kwance saida yayi jinkiri kaɗan kafin ya bata amsa da cewa "sosai ma hakan shi yafi sauƙi saboda na karya doka, bayan haka shuwagabanni nane suke son ganina amma naƙi zuwa, banaso wani abu ya taɓaki Yushert ga kinada juna biyu..." kuka Ayush ta fara yi ta riƙe hannun Junaid duk biyun tana faɗin "dan girman Allah Yaya Junaid kada ka shiga matsala saboda ni, ka ɗauke ni ka kai musu ni kamar yanda kayi musu alƙawari, ni inada tabbacin babu abunda zasuyi mun na zalunci, hukunci ɗaya ne shine nasan za'a kaini kotu ne, kuma nasan duk hukuncin da za'a yanke mun a kotu baza ayi mun yanzu ba dole sai an bari na haihu tukun, ka kwantar da hankalinka, haka kaddara ta tazo mun, kuma kowa baya tsallake ƙaddararsa saboda haka dan Allah ka tashi muje mu gurin aikin nakun, dan Allah badan ni..." shima binta da kallo yake kamar zaiyi kuka yace "Yushert ki barni dasu kawai". "a'ah ni kawai ka tashi muje mu, idan ma bakaje ba ni zan kai kaina..." tana ƙarasa maganar ta tashi da sauri ta nufi wardrobe ta zaro hijab ɗinta har ƙasa, ta sanya sannan ta fidda hannayenta waje ga ciki kuwa ya fito sosai... tashi yayi shima ya tsaya a gaban ta yana jinjina kai yace "shikenam tinda kin dage akan saina kaiki toh amma ki sani duk wanda yayi kokarin cutar mun dake wallahi wallahi saina ɗauki ƙwaƙwaran hukunci wanda kare ma bazai shanshana ba...". yana kaiwa nan ya riƙo hannunta ya kuma cewa "muje mu." yana janta a haka suka sauƙa falo shi kuwa yana sanye da baƙar jallabiya a jikinsa, suna fita out side na gidan suka shiga motar a hankali ya karya ƙwana sannan ya miƙi hanyar gate, kafin ya iso mai gadin ya buɗe musu suka fice da gudu..." ***** A sashin mommy Kuma kulawa iya kulawa tana samu agurin sarki Raamud, ga mata zaƙa² dake mata ayyuka, ko ƙwaƙƙwaran motsi mommy tayi sai sun tambayeta ko akwai abunda take so, ga ta ɓangaren sarki Raamud shima babu abunda zata nema ta rasa, wani ƙyakykyawar alaƙa ne a tsakaninsu duk da har yanzu babu maganar soyayya a tsakaninsu amma kana ganinsu kasan akwai ƙauna, yauma kamar kullum tana zaune akan dadduma dake wajen lambu a bayan masarauta ta ɗan shigingiɗa kaɗan tana riƙe da apple a hannunta har ta ci rabi, a gabanta kuma ƙaton paranty ne yana ɗauke da kayan fruits a ciki duk anyi slaces ɗinsu, ga kuma kuyange a wajen su biyar suna taya mommy hira, wasu suna mata tausa wasu kuma suna zazzaune kawai, dake suma ƴan aikin suna son kasancewa da mommy domin tanada son mutane, bata son zama ita kaɗai, suna cikin hira saiga mai martaba sarki Raamud ya shugo filin lambu dake fakaice guri guda, yana zuwa ƴan aikin suka tashi suna gaishe shi tareda ficewa daga wajen, shima zama yayi akan daddumar yana fuskantar mommy da murmushi a fuskarsa yace "Rankiya daɗe sarauniya na gaisheki..." murmushi tayi itama ta tashi zaune tace "haba mai martaba nifa ban zama sarauniya ba..." dariya yayi yace "ai kin zama mah" ta ɗago tana kallonsa tace "taya kenam?..". yace "saboda kema jinin masarauta ce..". zaro kyakkyawar idanuwanta tayi tace "o-oh o-oh! yara nane jinin sarauta bani ba, ban haɗu da masarauta ba" sarki Raamud ido kawai ya kafa mata da ƙyakykyawan murmushinsa yace "gashi kuwa yanzu ta dalilin yaranki kin zamo ƴar sarauta..." dariya tayi tana kawar da fuskarta gefe, yace "amma fah kinyi kyau sarauniya, alkebbar tayi miki kyau.." da sauri ta jawo mayafinta tana rufe fuskar, hannu yasa yana ƙoƙarin buɗe fuskar har yayi nasarar janye mayafin, ta sunkuyar da kanta ƙasi cikin jin kunya tace "dan Allah ka daina, mu ba yara ba..." yace "yaran to me suka iya in banda shirme, ai iya soyayya sai tsofi.." zaro ido mommy tayi tace "soyayya kuma?.." shima jin abunda tace ne yasa shi sosa ƙeyarshi yana faɗin "a'ah badai soyayya ba, wasa nake miki" tace "ohooo yanzu naji batu..." daga nan kowa yayi shuru babu wanda ya ƙara ce wa kowa komai, shi sarki Raamud tunaninsa ya zai fara sanar wa mommy cewa yana sonta, kuma gashi yana da burin Auranta, shi ason ransa ko yanzu ta amince masa zai iya sawa a ɗaura masa Aure a gobe domin har sauran masarantu sun fara complain akan wai sarki Raamud yana zaune akan mulki ba mata, su a tsarinsu duk wanda zai zauna akan mulki sai yanada matar Aure, ansha kawo masa ƴaƴan sarakuna akan ya zaɓi matar Aure amma yaƙi zaɓa shi idonsa nakan mommy Kuma ya kasa sanar mata, a tunaninsa bazata yadda bane, itama mommy gaba ɗaya hankalinta yana kan sarki Raamud, ganinsa take kamar mijinta, a duk lokacin da suka fake guri ɗaya kamar yanzu sai tayi tunanin kamar da mijinta take tare, har mantawa take da mijinta ya mutu saboda ganin sarki Raamud take kamar shi, domin kamar su ɗaya sakk kamar an tsaga kara, a duk lokacin da take kallon sarki Raamud bata sanin Lokacin da murmushi ke zo mata, kuma saita tsinci kanta a cikin farin ciki, ga kulawar da take samu a wajensa, amma wasu lokuta idan ta tuno da yaranta saita ji ba daɗi a ranta, yanzu ma Junaid da Ayush ne suka faɗo mata arai, sarki Raamud ganin hawaye a fuskar mommy ne yasa shi firgita da sauri yasa hannu ya tallafo kanta yana faɗin "sarauniya lafiya kuwa? meya faru dake kodai na ɓata miki ne, dan Allah kiyi haƙuri! ki sanar mun abubuwan da bakyaso da kuma abunda kike so, ni kuwa insha Allahu zanyi ƙoƙarin ganin na faranta miki.." murmushi tayi ganin yanda ya rikice akan ta, ta ɗago tana kallonsa tace " a'ah ba abunda kayi mun, kawai dai ina tunawa da yarana ne, bansan a wani hali suke ciki ba, dan Allah inaso naje garesu..." Sarki girgiza kai kawai yayi ba tareda yace komai ba, sai bayan ya ɗanyi jinkiri tukun yayi ajiyar zuciya yace "kuyi haƙuri sarauniya, insha Allahu zaki gana dasu! inaji ajikina suna nan cikin ƙoshin lafiya.." mommy ɗagowa tayi kamar zata fashe da ihu tace "ni kawai inason sanya su a cikin idanuwana" murmushi yayi yace "shikenam ki ƙwantar da hankalinki zuwa end of the month zamu tafi Nigeria tare...". sai a wannan lokacin mommy tasau ƙayataccen murmushi ta ɗago suna kallon juna... ****** misalin ƙarfe 12 na rana motar Junaid ta ƙaraso cikin babban harabar cikin headquarter wanda yake zazzagaye da sojoji, parking yayi sannan ya fito jikinsa a sanyaye yasa hannu ya fito da Ayush jikinta sai faman kakkarwa yake ganin manya² sojoji suna riƙe da bindigu ga babu alamar wasa a fuskarsu, riƙo hannunta yayi suka nufi ciki, suna zuwa wasu sojoji suka tare hanyar shiga asalin cikin compound, tsayawa yayi yana kallonsu cikin ɓacin rai yace "Lafiya kuwa zaku tare mun hanya?.." suka ce "Ance kada mu barka ka shiga ciki da zaran kazo..." Junaid cike da mamaki ya kuma cewa "and what is your reason?.." haɗe baki sukayi waran cewa "Sorry Ogah umarni ne daga waran General..." jinjina kai Junaid yayi tareda faɗin "okay fine.." har ya juya zasu nufi wajen motar suka ji daga sama ance "Captain Junaid come up we want to see you..." Junaid daidaita tsayuwarsa yayi yana kallon saman stairs ya amsa da "Okay Sir..." kallon Ayush yayi sannan yace "wait for me I'm coming back..." da sauri ya wuce ya fara taka matakala har saida yaje gidan beni mai hawa bakwai tukun ya shiga office ɗin da ake son ganinsa, Shigarsa ya juma sosai aciki kafin ya fito hannunsa riƙe da farar takarda, fuska ba Annuri cikin fushi ya soma sauƙowa down stairs, laifin da ya aikata zaɓi biyu aka bashi a matsayinsa na Captain, sanar masa akayi koya zaɓi zaman gadurum na tsawon kwana biyar ko kuma a bashi takardar sallama, already karɓar takardar sallama yayi saboda gani yake yafi ƙarfin zama a gadurum kuma bayan haka yaransa sojoji zasu raina shi ne, shidai ya karɓi takarda saboda yasan daga baya zasu mayar dashi bakin aikinsa domin Junaid yana musu aikin da ba kowani soja ne zai iya ba... Bayan ya sauƙa ƙasi gani yayi an ɗauke Ayush babu ita a wajen, waige-waige ya fara yi yana tambayar sojojin wajen, da hannu suka nuna masa yanda marshal yake a cikin ƙatuwar motarsa yana ta faman danne² wayansa, da gudu Junaid ya nufi wajensa yana faɗin "please Sir where is my wife?..." Marshal ko ɗagowa baiyi ya kalle shi ba, durƙusawa Junaid yayi yana roƙonsa akan ya sanar masa ina aka kai Ayush ɗinsa, marshal gajiya yayi da jin surutan Junaid haka yasa ya fusata yana ɗaga murya yace ",you will shut up? meya zaunar dakai bayan an sallame ka? shin baka zaɓi barin aikinka ba? ka kasa cika alƙawari, matarka nasa an kamata tana can cikin maƙarƙama a ɓoye, dole sai hukuma sun hukuntata...". Junaid kamar zaiyi ihu yace ", please officer inason sake sanyata acikin idanuwa na Please..." Marshal yace "munga tana da juna biyu ne yasa muka sassauta mata amma badan haka ba sawa zanyi a kakkarya mata sawaye, saboda haka bazaka taɓa ganinta ba saidai ku haɗu a kotu...." Zaro ido waje Junaid yayi duk yabi ya jiƙe jikinsa da gumi sai a yanzu yayi nadamar kawo Ayushh.... *DAN ALLAH KUYI HAKURI MATAR DAMISA FANS, WLLH INA WANI AIKI NE TIN ASUBA MUKE FITA BANA DAWO GIDA SAI DARE, TOH LOKACIN A GAJIYE NAKE GA DA WURI NAKE BACCI* *AMMA INSHA ALLAHU DAGA YAU MUN GAMA, YANZU MAH WANI IRIN MASIFAFFEN BACCI NE YAKE DAMUNA SHIYASA NA HAƘURA DA YIN TYPING HAKA SAI ZUWA GOBE, GOBE BA KOMAI ZANYI BA ZANYI MUKU UPDATE AMMA GA WANNAN KU RAGE DUK DA NASAN YAYI KAƊAN SOSAI AMMA KUYI HAKURI 🙏🙏🙏* 𝑡𝑦𝑝𝑖𝑛𝑔✍️ 𝗠𝗔𝗧𝗔𝗥 𝗗𝗔𝗠𝗨𝗦𝗔 the wife of a tiger🐅🐅🐅🐅 𝙼𝚊𝚕𝚕𝚊𝚔𝚒𝚗 𝙰𝚜𝚖𝚎𝚎𝚝𝚊𝚑 ✍️✍️ 𝙿𝚊𝚒𝚍 𝚋𝚘𝚘𝚔 𝚌𝚊𝚕𝚕 𝚘𝚛 𝚠𝚑𝚊𝚝𝚜𝙰𝚙𝚙 09065443871 *💫💫{{N W A}}💫💫* Book two C̶h̶a̶p̶t̶e̶r̶ 55 ➡️ 56 Junaid a fusace yake driving motor kamar zai tashi sama bai samu ganin Ayush ba da haka ya ƙariso gida, ita kuma Ayush cikin wani ɗaki aka kaita na tsaro, ɗaki ɗaya ne amma saidai akwai katifa da wasu abubuwan da baza'a rasa ba, ɗakin yayi kyau, sai wani soja da yake tsaye ta wajen ɗakin yana gadinta! tana ƙwance ta haɗe kanta da gwiwa sai faman rera kuka take a haka ta wuni tana wannan kukan, ji tayi an buɗe ɗakin da sauri ta ɗago tana kallon bakin ƙofa a tunaninta Junaid ne sai kuma taga wani soja ne daban ya shugo da kular abinci, ya ajiye a gabanta yana faɗin "ki tashi ki ci abinci da zaifi miki.." bata kula shi ba saima ƙara ƙarfin kukan da take yi, shi kuwa miƙe wa yayi ya fice daga ɗakin... washe gari Junaid ne yaje gidan malam Lawan ya kora masa bayanin abunda ke faruwa ya kuma cewa "dan Allah malam ka temaka mun Yushert ta dawo hannu na, matata ce kuma sannan tana da juna biyu bai kamata ace tana hannun sojoji ba, ni nariga da nasani akwai ƴan iska acikin su, banaso wani abu yazo ya faru domin nasan dole zanyi kisan kai duk wanda ya taɓa mun matata.." malam Lawan idonsa akan Junaid yana girgiza kai yace "insha Allahu ba abunda zai faru, kuma ina tunanin sun shigar da ƙara a kotu tin ba yau ba, yau kuma za'a shiga shara'a, ni a halin yanzu babu abunda zan iya amma zan tura ka gurin abokin mahaifinka wato Barrister Aminu insha Allahu zai tsaya maka.." girgiza kai Junaid yayi yace "ba lallai ba domin nasan bazai goyi bayan Yushert ba, saboda ba zarginta ake yiba ta tabbata da gaske ta kashe mahaifiyata, kowa yasan da hakan, dole nasan sai an yanke mata hukunci sakamakon hujjojin da ake dasu, ban san yazanyi ba .." Malam dafa kafaɗarsa yayi sannan yace "ka kwantar da hankalinka insha Allahu za'a dace, amma Ayshert ta aikata babban kuskure sai dai kawai ka dage da addu'a ka kuma ƙara da haƙuri..." Junaid miƙewa yayi da sauri yana faɗin "kafin a tafi da ita zanje na ganta, dole sai naga matata ko kuma ran kowa ya ɓaci domin bazan juri rainin hankali ba..." yana kai ƙarshen maganar yayi ficewarsa, kai tsaye headquarter ya nufa da motarsa.. Ayush tana zaune akan katifa ta haɗe kai da gwiwa kamar mai yin bacci amma sai dai akwai tunanin da take yi, wani soja ne ya shugo cikin ɗakin da saurinsa sannan ya mayar ya rufe ƙofar, tsayawa yayi yana ƙareta da kallo tareda cije lips ɗinsa, muryarsa kamar wanda yayi maye yace "ke ƴan mata ki shirya yau zaki haɗu da mutanen kotu, yanzu haka nazo tafiya dake ne ana jiranki, ki sani hukuncin ki kisa ne kamar yadda kema kika yi kisan kai amma kafin ki mutu zan ɗanyi koɗuma dake ko zanji sanyi², tinda aka kawo ki nake jin ƙwaɗayinki please kiban haɗin kai yanzu zan gama, bamai kallon mu..." ita kuwa tana jinsa ko ɗagowa batayi ba, ita kaɗai tasan irin takaicin da take ji, yanayin maganarsa na rashin ɗa'a ba ƙaramin ƙona mata rai yayi ba, durƙusawa yayi a gabanta ya ƙara matsowa daf da ita yana mata wani irin kallo tareda fitar da harshensa yana lasan lips ɗinsa, hannu ya ɗago ya dafa kafaɗarta, ɗagowa tayi a fusace ta zazzaro manya-manyan idanuwanta tana kallonsa, ido yayi jawur duk da wannan kallon da take yimasa baisa ya janye hannunsa ba saima shafata da yake yi yana washe baki tareda faɗin "wayyo ƴar fara ƙyakykyawa, mai zubin halitta irin na ƴan aljanna...". yana shafata har zuwa wuyanta! Ayush idonta ta sauƙar kan wuƙar dake sokare cikin takalminsa da sauri takai hannu ta zaro wuƙar ta sauƙar da hannunsa wanda yake shafata dashi ta datsa masa wuƙar a hannun duk saida ta cire masa yatsun hannu guda huɗu, baisan lokacin da ya fara kurma ihu ba, kafin kace mai jini ta ko ina, ga kuma yatsun hannu a yaje a ƙasi, yana riƙe da hannu sai ihu yake yana neman agaji, ita kuwa kifar da kanta tayi kan gwiwarta kamar yanda take a farko ko sauraronsa bata yi ba saima toshe kunnuwanta datayi da hannu biyu, da ƙarfin gaske aka bankaɗo ƙofar ɗakin sojoji ne waran su shida suka zo jin ihun da ake yi, abunda suka tarar ne ya basu mamaki, ɗago da majinyacin sukayi suna tambaya meya faru dashi ne amma ya kasa basu amsa sai nuna yatsunsa da yayi a ƙasi, zaro ido sukayi ganin yatsu a ƙasi ga jini duk ya wanke wajen, kallon yanda Ayush take zaune sukayi ko ɗagowa batayi ba balle abun ya dameta... ɗaya daga cikin sojojin ne yaje gaban Ayush a fusace yasa hannu ya riƙo damtsenta ya ɗagota tsaye a tsawace yake faɗin "kee me kika aikata masa? kin zamo ƴar ta'adda koh?..." harararsa tayi fuska a haɗe tace "ka sakar mun hannuna ni matar Aure ce..." ɗago hannu yayi zai mareta wani daga ciki yayi saurin riƙe hannun yace "a'a Commander ka ƙyaleta yanzu haka kotu za'a tafi da ita, zatayi bayani..." Ayush tarar bakinsa tayi da cewa "kafin aje kotu ma zanyi bayani saboda wannan case bana kotu bane..." tana kaiwa nan tayi ficewarta wani soja yana biye da ita a baya, Ƙwafa Commander yayi yana nuna ta da yatsa yace "wannan yarinyar wallahi badan Captain Junaid ba da ba abunda zai hana na buga mata bindiga a kayinta..." ya ƙarisa maganar tareda riƙe abokin nasan wanda aka yankewa yatsu ya fita dashi, ɗayan sojan kuma kwashe yatsun yayi a farar leda shima ya fice.. Ayush ce a gaban General da Marshal da sauran sojoji masu manyan miƙami da kuma ƙananun sojaji duk suna tsaye bayan sanar musu da abunda Ayush tayiwa ɗaya daga cikin sojoji, a tsawace General yake tambayarta dalilin da yasa tayi haka, amma Ayush tayi shuru babu bakin magana kai a sunkuye sai faman kuka take, daiden lokacin da Junaid ya shugo da motarsa da gudu, da sauri yayi parking ya fito ganin yanda aka taru ga kuma Ayush a durƙushe a rana, da gudu ya iso gurin baiyi magana wa kowa ba sai nufan gurin da Ayush take yayi, yana zuwa yasa hannu ya ɗagota tsaye yana goge mata hawayen fuskarta da hannu, ji yayi Marshal ya darara masa tsawa tareda faɗin "umarnin wa kabi ka ɗago da ita? shin meye matsayinka a yanzu da har zakayi mana wannan shishshigin...". Junaid bai kulashi ba yana kallon Ayush yace "Yushert what happened to you?.." kuka ne yaci ranta sosai tasa hannu ta rungume shi, shima rungumarta yayi rai a ɓace domin baiji daɗin ganin Ayush a wannan yanayin ba, General ne ya katse shi da cewa "Junaid mai kakeyi haka, waya baka izinin shugowa wannan quarters?..." kallonsa Junaid yayi sannan yace "sorry Sir but what happen to my wife? meyasa zakuyi mata wannan hukunci? ku bari kotu ta yanke mata hukunci ba ku ba..." Marshal yayi saurin katseshi da cewa "kaii ka kama bakinka, kasan da wanda kake yiwa magana, General ne a gabanka..." Junaid cikin fushi ya dakawa marshal tsawa da cewa "and so whattt? banda Allah babu wanda nake jin tsoro saidai nayi biyayya nabi dokar aiki." ya ƙarasa maganar tareda kallon yanda canal yake yace "tell me what's going on?..." Canal nuna naseer yayi da yatsa yace "matarka ce ta yanke masa yatsu guda huɗu..." Junaid ya kalli Naseer yace "whatt? amma me yayi mata?.." Canal yace "muma bamu saniba yaƙi yin magana kuma itama taƙi cewa komai" Junaid ɗago da Ayush yayi daga jikinsa yana kallonta yace "Yushert!.." ɗagowa tayi tana kallonsa itama ya kuma cewa "meya haɗaki dashi? kar kiji tsoron kowa ki buɗe baki kiyi magana babu abunda zai faru dake, ko waye bai isa yayi miki abunda Allah baiyi niyar miki ba..." Ayush murmushi tayi ta ɗanyi nisa da Junaid kaɗan kafin ta ɗaga murya tana faɗin "Yaya Junaid ba wai tsoron su ne ya hanani yin magana ba, kawai dai inaso nayi magana ne a gabanka ka duba mun shin Abunda na aikata daidai ne ko kuskure...." ta kalli sojan ta nuna shi da yatsa tace "wannan mutumin idan shine zai riƙe ƙasa toh tabbas duniya bazata zauna lafiya ba, idan yasu ne zasu kare ƙasa toh kuwa saidai ayita mutuwa domin basu da wani daraja da kima, sannan basu san mutuncin mace ba, idan kuwa zasu iya lalata rayuwar mace to kuwa zasu iya yin lalata da mahaifiyarsu, idan kuwa haka sojoji suke Allah ya wadaran su, idan haka soja yake bashida imanin da zai tausayawa mace ko yaro ko tsoho toh Allah ya tsine masa aikinsa bashida wani amfani, sai gadarar riƙe bindiga..." Marshal ne ya katseta da cewa "kee ba'a ce kici mana mutunci ba don kina gaban mijinki to karki manta shima mijin nakin ai soja ne..". Ayush tana fuskantar Marshal tace "ehh mijina soja ne amma ba irin lalatattun sojojin nan ba kamar waɗanda suka tsargu..." Marshal ne zai nufo gurinta cikin zafin nama yana cewa "ke karfa kimun rashin kunya domin mijinki ma da kike gadara dashi a ƙasana yake yanzu kuwa an sallame shi gaba ɗaya bakuda bakin magana..." General ne ya dafa kafaɗansa yana masa alamar sauƙowa..." Junaid murmushi yayi yana kallon Ayush domin ba ƙaramin burgeshi tayi ba, yanzu babu wannan tsoron natan, zata iya tsayawa a gaban kowa tayi magana, yace "Yushert colm down kije kan maganarki kai tsaye..." alamar voting tayi masa sannan ta cigaba da cewa "ina zaune yazo yana mun magana cikin rashin ɗa'a da daraja, a matsayina na mace kuma matar Aure shin ya kamata yayi mun maganar fasiƙanci? a'ah abun ya wuce fatar baki har hannu ya kawo yana shafa mun jiki da sunan saina biye masa yayi lalata dani, hakan yasa na yanke masa yatsun hannu saboda na koya masa darasin rayuwa...." Junaid a zabure yace "whattt?..." zuwa yanda take yayi yasa hannu ya zabga mata mari ya riƙe mata kafaɗu da hannayensa biyu yana fuskantar ta rai a ɓace cikin ɗaga murya yace "hakan shine abun burgewa?..." sauran sojojin da suke wajen abun ya ɗaure musu kai ganin yanda Junaid yake ganin laifinta, suna cikin wannan tunanin suka ji yace "amma kin cuceni Yushert, naso ace wuƙar da kika zara caka masa kikayi a maƙogaro, meyasa zaki tsaya a iya hannu? meyasa baki yanke masa wuya ba?..." kamar zaiyi kuka haka yake jijjiganta... wanda aka yankewa yatsu ne ya soma magana cikin kakkarwar murya yace "wallahi ƙarya take...." kafin ya rufe baki Junaid yayo sufa kamar Damisa ya cabke masa wuya, da iya ƙarfinsa yake matse masa maƙogaro har saida yakai shi ƙasi, duk sojojin wajen ne suka rufu akan Junaid suka ƙoƙarin janye shi amma sun kasa, wani irin ƙarfin bala'i ne da Junaid, ko girgiza bayayi tsabar ƙarfinsa daya danna akan wuyan Naseer, haka yake kakakin mutuwa ido sun fito waje, sai shure-shure yake numfashinsa a ɗage cakk, Junaid yana ƙoƙarin murɗe masa wuya akayi saurin kawo Alluran macewar jiki da sauri aka caka masa, daga nan ne akayi nasarar janye shi daga kansa, shi kuwa Naseer tinin ya suma kaɗan ne ya haka ya mutu domin inda anyi kuskuren jinkirin kawowa Alluran nan da Junaid ya karya masa wuya... Junaid gaba ɗaya ya fita hayyacinsa sai cewa yake "ku barni na kashe shi, ku ƙyaleni nace, gaba ɗayanku zan kashe ku idan baku sakeni ba, zan kashe ku! zan kashe ku!! zan kashe kuuu!!!..." da haka shima ya sume a wajen sakamakon temporary da jikinsa ya ɗau ga kuma Allurar da aka masa, sai a lokacin sojojin suka sake shi tareda ɗaukarsa suka nufi cikin ɗakunan quarters dashi... Junaid wani irin zuciya ne dashi wanda lokaci guda hankalinsa zai bar jikinsa da zaran ransa ya ɓaci matuƙa, kuma ƙarfinsa ƙaruwa yake a lokacin, dake Jinn sun shafeshi tin lokacin da sarki Raamud yake turo masa su, bayan hakan jinin tiger ya rigada ya gudana da jininsa dole da zaran ransa ya ɓaci abun zai ɗan motsa masa, amma ba kamar baya ba... shiyasa General baya shiga sabgarsa sosai saboda gudun ɓacin ransa, iya marshal ne kawai yake fafatawa da Junaid dake shima yanada zafin rai amma bai kamo ƙafar Junaid ba... Bayan shigar da Junaid cikin room marshal ne ya damƙi damtsen Ayush ya shigar da ita cikin mota shima ya zagaya ya shiga da gudu ya finciki motar suka tafi kai tsaye kotu suka nufa, sai kuma wasu motocin sojoji da suka biyo bayansu, Naseer kuma hospital aka kai shi. Bayan 10hours an gama Shari'a! malam Lawan ma ya halacci kotun, ba'a yanke hukunci ba amma an bada horo ɗaya, Ayush zata zauna a gidan gyaran hali har ta haihu, bayan ta haihu ne za'a sake zama a kotu anan za'a yanke hukunci, Bayan an fito da Ayush za'a tafi da ita prisoner faɗuwa tayi ta fara burburwa a ƙasi tana juyi tareda zunduma ihu, wasu mata ne suka rirriƙeta suna shirin ɗagota amma sam taƙi shiga cikin mota, kamar wata mai Aljanu haka take ihu tana faɗin "wallahi bazanje prison ba! wallahi bazanje prison ba, wayyo Allah nah Yaya Junaid, nashiga uku ku temake ni wayyo Abbanaaa, Ummanaaa..." kokuwa take dasu tana kai musu duka suma haka suke janta, ganin matan bazasu iya shigar da ita cikin motar ba yasa soja ɗaya yazo ya kimkimeta, shima haka take yakushinsa tana cizonsa tana kurma masa ihu da haka ya sakata a cikin motar aka rufe da ƙarfi, har aka tada motar suka tafi da ita tana wannan ihun, har muryarta yana shirin dishewa, fuskarta duk ya yi jawur tsabar kuka, Malam Lawan yana tsaye a gurin saita yayi hawaye shima rai a jagwalgwale ya shiga motarsa ya tafi... Acan ɓangaren Junaid kuma farfaɗowa yayi yana ambaton sunan Yusherttt gani yayi babu kowa a cikin ɗakin da aka ƙwantar dashi, tsararren ɗaki ne na hutawar manya-manyan sojoji ga sanyin A.C yanda yake ratsa shi ga kuma mashigar toilet ta gefe guda, da saurinsa ya tashi ya nufi bakin ƙofa zai buɗe ya fita, cike da mamaki yake bin ƙofar da kallo ganin an kulle ta waje, babu hanyar fita, da ƙarfi yasa hannu ya naushi ƙofar tareda yin ihu a fusace, ganin ƙofar bazai buɗu ba yaje ya samu guri a bakin gado ya zauna tareda dafe kayinsa da hannayensa biyu yana kallon ƙasi.... yana nan a haka har dare basu zo sun buɗe masa ba, kuma suna jin yanda yake ta buga ƙofar yana ƙiraye-ƙirayen sunayensu amma babu wanda yaje ya saurare shi domin bin umarnin Marshal, shi ya sanar musu cewar kada su kuskura su buɗe masa ɗakin har washe gari, saboda yana tunanin zaije ya ɗauko Ayush ne da zaran an barshi... ******* Ayush tana zaune acikin ɗakin da aka ajiyeta, ɗakin sun kai su goma aciki kowa da shimfiɗarsa kamar boading skull, ga an sauya mata kayan jikinta ya koma irin na sauran ƴan matan prison riga da wando iri ɗaya kowa da number a jikin rigarsa, kowa yana ƙwakkwance amma banda Ayush wacce take zaune a shimfiɗarta sai rera kuka take sakamakon yanzu dare ne misalin ƙarfe 12Am, duk ta cika musu kunne da kuka wata mata ce ta taso a zabure tayo kan Ayush tana masifar cewa "ke duk kin hanamu bacci, bama son sakalci fa kowa ma ba son zaman nan yake ba, dan haka ki rufe mana baki ko kisha mazga yanzun nan...." Ayush ko sauraronta batayi ba saima ƙara volume ɗin kukan take, matar ce ta ɗagota tareda zabga mata mari har sau biyu tana faɗin "wallahi tallahi zan fitarki waje kika ƙara mana kuka .." Ita kuwa Ayush tinin ta haɗiye kukan ta sai hawayen dake zubo mata ba ƙaƙƙautawa, ɗaya ce daga cikin prisoner girl tace "haba Mimi ki ƙyaleta mana bakiga tanata juna biyu bane, kiyi mata uzuri dan Allah, kowa ma farkon zuwansa haka yayi..." Mimi tace "bazan ƙyaleta ba Hafiza, idan kina mun shishshigi kema saina ci jatuminki, kina nam ƙarama dake sai iyeyin banza, ita kuma wannan idan na sake jin kukanta saina fasa mata baki wannan alƙawari nane babu ruwana na cikinta..." tana kaiwa nan ta ƙwanta a wajenta tana surutan ta har bacci ya kwasheta, Itama Ayush ƙwanciya tayi data ga ba wani sarki sai Allah duk da sauron dake ɗakin bai dameta ba saboda ta saba da zaman daji, batayi tsammanin zata zauna a prisoner ba. Washe gari duk matan prisoner kowa ya fito da kwanonsa suna zuwa yin layin karɓan abinci, banda Ayush dake ƙwance a ɗaki ta kasa motsawa sai kuka, wata yarinya ce tazo kusa da ita takai hannu tana tattaɓata da sauri Ayush ta ɗago tana kallonta, yarinyar tace "kina ƙwance ki taso muje mu karɓi abun breakfast..." daƙer Ayush take motsi da bakinta tace "bana buƙatar cin komai..." yarinyar tace "idan bakije ba babu wanda zai saurareki balle ya kawo miki har yunwa tayi miki illa, ni idan naje da kwano biyu bazasu bani ba ki daure ki tashi muje kodan jaririn dake cikin ki..." Ayush haka take bin yarinyar da kallo tana mamakin yanda akayi yarinya ƙarama tazo prison, gashi shekarunta bazata wuce 17 zuwa 18 ba, jinjina kai Ayush tayi tace "shikenam zanci ne saboda yarona..." haka ta tashi suka tafi tare da yarinyar har gurin karɓan abinci ga kayansu iri ɗaya mai launin sky blue.. Bayan sun karɓi abinci zama sukayi a wani waje su kaɗai yarinyar a hankali take feeding Ayush sakamakon yanayin abincin bazata iya ci ba saida dabara, Bayan sun kammala breakfast yarinyar ce ta soma magana tana bawa Ayush labarinta tace "Ni sunana Hafiza asalin ƴar Kano ce, iyayena talakawa ne futuk sai nayi tallah muke samun abinda zamu ci, ƙwatsam wani saurayi ɗan gidan attajirai ya ganni yace yana sona, ni kuma a lokacin inada wanda nakeso shima talaka ne amma saidai yanada ƙwalin degree ɗinsa amma babu aikin yi, ni kuma a iya sacondary na tsaya, iyayena suka tilasta mun akan saina Auri ɗan masu kuɗi bana sonsa haka akayi mun Auren dole dashi, ƴan uwansa basa son mu ƙyamatar mu suke suna ƙiran mu da ƙazamai, da haka akayi auren aka kawoni nan garin Abuja, a daren farko na dashi ban yadda masa ba, haka nake gudunsa, a cikin daren nan na fito daga cikin ɗakin dake upstairs ne ina sauƙowa ƙasi shima yana biyoni a baya kwatsam tsautsayi ya rubta dashi ƙafarsa ta zame daga saman beni ya buga kansa da tiles, lokaci guda kayinsa ya fashe bama iya fashewa bama tsagewa kayin yayi daga lokacin bai ƙara motsi ba rai yayi halinsa...." ta ƙarasa maganar tareda fashewa da kuka ta cigaba da cewa "shine ƴan uwansa sukai ta cewa ni na kashe shi wai, wallahi bani na kashe mijina ba, sun fimu arziƙi nesa ba kusa ba hakan yasa aka yanke mun hukuncin zaman gidan prison har tsawon ƙarshen rayuwata....". kuka ne yaci ranta sosai, Ayush itama kukan take domin ba ƙaramin tausaya mata tayi ba, gata ƙaramar yarinya, haka Ayush ta jawota jikinta tana rarrashinta, ita yanzu tama daina damuwa da kanta tinda a cikin prisoner har da ƙananun yara... *BAYAN WATA 3* Ayushert ta rigada ta sabarwa rayuwarta a cikin prisoner, yanzu ta daina damun kanta da yawan kuka, ga sun shaƙu sosai da Hafizat ta mayarta tamkar ƙanwarta ta jini komai tare suke yinsa, akwai abunda Hafiza bata barin Ayush tayi shine irin su wanki da ɗaukar abu mai nauyi duk Hafiza ke yinsu sakamakon cikin Ayush ya girma sosai, domin cikin yanzu watansa takwas, duk wasu ayyukan bauta da ake sakawa an bada umarnin kada a saka Ayush a ciki, yanzu hankalinta a ƙwance yake ba kamar farko-farkon zuwanta ba, kowa sai yace zai hantareta ita da Hafizat.. Damuwarta shine abu ɗaya wato Junaid tana mamakin yanda tsawon watannin nan amma baizo ya dubata ba, kuma sai take zargin anya lafiyarsa ƙalau, shine kawai damuwarta, amma malam Lawan yakan zo mata wasu lokuta, tana tambayarsa Junaid amma sai ya sanar mata cewa yana nan lafiya ƙalau, a yau ne daya zo yake sanar mata cewar tin lokacin da aka kawo ta prison Junaid yake kulle a gurin mutanensa sojoji, Ayush tasha kuka sosai jin haka.... ****** Duk tsawon wata ukun nan Junaid yana kulle a ɗakin dake quarters, Marshal yaƙi bari a fito dashi wai sai matarsa ta haihu a prison tukun, Abinci kuwa sai an daideci yana bacci tukun a buɗe a hankali a ajiye masa tukun a sake kulle ɗakin, shima haka rayuwarsa yake tafiya shi kaɗai a cikin ɗaki, zaman kaɗaici ya dameshi ga wayarsa tana hannunsu, yayi masifar! yayi barazana!! yayi magiyar!!! yayi kukan har ya gaji, ga yanaso ya sanya Yushert ɗinsa a ido amma babu hali, yayi matuƙar kewar matarsa Yushert, shi kaɗai yasan kalar raɗaɗin da yake ji a cikin zuciyarsa, sannan ya ƙudurta a ransa cewar da zarar ya fito duk saiya ƙona headquarters ɗin gaba ɗaya, babu abunda zai rage a cikinta tinda har zasu masa wannan wulaƙanci da tozarci... Malam Lawan yayi zirga-zirga wajen sojojin nan akan subar masa Junaid ya tafi dashi amma sun ƙi da haka har ya gaji ya daina zuwa, ****** Ata ɓangaren mommy da sarki Raamud sunata shirye shiryen dawowa Nigeria, duk da basu san abubuwan dake faruwa ba, Mommy murna kamar bazata mutu ba tana son dawowa gurin yaranta, ga tayi missing ɗin Junaid ɗinta, sun yanki Visa gobe da safe jirginsu zai tashi... *TEAM ƊIN JUNAID DA TEAM ƊIN AYUSH NACE BAA HOW MARKET 🤪🤪🤪🤪🤪🤪🤪* 𝑡𝑦𝑝𝑖𝑛𝑔✍️ 𝗠𝗔𝗧𝗔𝗥 𝗗𝗔𝗠𝗨𝗦𝗔 the wife of a tiger🐅🐅🐅🐅 𝙼𝚊𝚕𝚕𝚊𝚔𝚒𝚗 𝙰𝚜𝚖𝚎𝚎𝚝𝚊𝚑 ✍️✍️ 𝙿𝚊𝚒𝚍 𝚋𝚘𝚘𝚔 𝚌𝚊𝚕𝚕 𝚘𝚛 𝚠𝚑𝚊𝚝𝚜𝙰𝚙𝚙 09065443871 *💫💫{{N W A}}💫💫* Book two C̶h̶a̶p̶t̶e̶r̶ 57 ➡️ 58 Today is Monday Around 2pm jirgin su Mommy suka sauƙa a Nigeria, Mommy murna kamar bazata mutu ba har ɗaukin ganin yaranta take kamar zata fura, Allah! Allah take ta isa gida, sarki Raamud ya fahimceta duk wannan saurin so take taje gida murmushi kawai yayi ba tareda yace komai ba, shima kansa mamakin kansa yake yana maganar zuci "wai yau nine a Nigeria? Allahu Akbar Aure mai haɗa zumunta...". suna tafe a motar haya domin babu motar a hannunsu, har suka ƙariso ƙofar gida, ganin yanda gidan ya rurrushe yayi baƙi ƙirin yasa mommy cewa "Yaa Salam haka gidana ya koma? kuma Junaid baiyi ƙoƙarin gyarawa ba? toh yanzun acikin gidajensa wanne ɗaya ya koma sai Allah...." Sarki Raamud shima kansa abun ya bashi mamaki ganin yanda gidan ya ƙoƙƙone, baiyi tunanin har abun yakai haka ba yana jinjina kai yace "yanzu ya za'ayi mu samu Junaid?.." Mommy ta juyo tana kallonsa cikin nuna damuwa tace "yanzu haka idan nace zan sauƙa nayi tambaya sai suce zasu firgita domin a tunaninsu na mutu ne, ni kuma nafison nabi abu a sannu har su gane cewar ba mutuwa nayi ba..." Sarki Raamud shima idonsa akanta yace "hakane toh amma yanzu meye abun yi?.." da sauri mommy tace "ahh! muje gidan malam Lawan..". cikin rashin fahimta yace "waye malam Lawan kuma?..." Mommy tace "idan muka je zaka ganshi, daga nan sai in baka labarinsa" murmushi yayi sannan yace "okay..." suka sa mai motar ya juya mommy tana masa ƙwatance har suka isa gidan malam lawan... Bayan isar su gidan suka tarar dashi shima ya fito daga cikin gidansa da motarsa alamun wani guri zaije, ganin mutane a tsaye da akwatunansu mata tana ɗaga masa hannu, cike da mamaki ya buɗe murfin motar ya fito sakamakon rashin gane kosu su waye ne, da sauri mommy ta nufi wajensa tana murmushin farin ciki, ganinta yasa malam Lawan tsorita da sauri yake ja da baya yana furta "innalillahi wa inna ilaihi raju'un, wacece kamar Hajia Fateema?..." Mommy tsayawa tayi tana kallonsa daman tasan hakan zata faru, kafin su yadda da ita sai ta fahimtar da su tace "please malam Lawan kar ka tsorita dani dan Allah, wallahi nice Doctor Fateema ban mutu ba da raina..." cike da mamaki ya sake maimaita cewar "baki mutu ba?..." ɗaga masa kai tayi tana murmushi, sauƙe ajiyar zuciya yayi sannan yace "toh amma ya akai kika tsira kuma?.." Mommy tace "kafin kamun waɗannan tambayoyin ka fasa zuwa ko ina mu shiga cikin gidan..." Malam Lawan ya ɗaga kai yana kallon mutumin da yake tsaye gefe guda yace "wancan fah kice masa ya iso cikin gidan..." yana kaiwa nan ya buɗe gate suka shiga daga ciki kai tsaye babban falo ya nufa dasu, a falon ya tarar da matarsa ya sanar mata cewar ta haɗo kayan abinci da drinks, yana tsaye saiga Mommy ta shugo da sallama a bakinta ya amsa mata cikin kulawa sannan ya nuna mata waran zama tareda tsokananta yana faɗin " Allah dai yasa ba Aljana bace ta fito a suffar Hajiya Fateeman mu...". ya ƙarasa maganar tareda zaunawa shima, dariya abun ya bawa mommy tace "in ma Aljana ce ai baza a guji mai suffar Hajiya Fateema ba..." Daiden lokacin da Sarki Raamud shima ya shugo da sallama a bakinsa, ganin sarki Raamud yasa malam Lawan miƙewa da sauri yana kallon sarki Raamud, a ruɗe yace "Raamud?...". shima sarki Raamud tsayawa yayi yana kallon Malam Lawan cike da mamaki shima ya ambaci sunansa da cewa "Artaf daman kana duniya?..." malam Lawan kallon mommy yayi sannan ya maida idonsa kan sarki Raamud yace "za zauna mana, nasan ka juma baka ji labarina ba shiyasa kake tambaya ko ban mutu ba daman, amma ni nasan kana nan amma ban taɓa tunanin zaka zo Nigeria ba..." Sarki Raamud zama yayi tareda bashi amsar "eh nazo Nigeria ne saboda ƴaƴana amma ba jumawa zan koma saboda masarauta.." Malam Lawan yayi murmushi haƙiƙa yaji daɗin maganar sarki Raamud yanzu ya ƙara tabbatarwa da cewar ya shiryu ya kuma rungumi Junaid a mazannin ɗansa... Mommy dai sake baki tayi tana kallon ikon Allah baki na kakkarwa tace "am am daman kunsan juna ne?..." jinjina kai malam Lawan yayi yana kallon mommy yace "ata sanadiyar wa kika Sanni?.." tace "ata sanadiyar marigayi mijina..." ya kuma cewa "okay meye matsayin wannan agurin mijinki?.." ya ƙarasa maganar yana nuna sarki Raamud, Mommy tace "shi ɗin ɗan uwansa ne" malam Lawan yasau ƙayataccen murmushi sannan yace "toh kinga kuwa akwai kyakkyawar alaƙa dake tsakanin mu, domin ni ɗin ma ɗan cikin masarauta ne..." Mommy ta zaro ido waje cikin ɗaga murya a ruɗe tace "tayaya hakan zata faru?..." malam Lawan yace "ki ƙwantar da hankalinki zan sanar miki amma sai mun haɗu gaba ɗaya dasu Junaid..." Mommy kallonsa take kai kawai ta ɗaga mashi gaba ɗaya ta shiga cikin zullumi, Sarki Raamud ne yayi magana tareda faɗin "ina su Junaid ne?.." sauƙe numfashi malam Lawan yayi yana girgiza kai yace "wato abunda ke faruwa shine!. duk abubuwan daya faru saida ya ƙwashe tas ya sanar musu, Hankalin mommy ba ƙaramin tashi yayi ba jin irin ƙalubalen da yaranta suka shiga Kuma duk ata sanadiyar ta, dafe goshi tayi tana faɗin "innalillahi wa inna ilaihi raju'un, Ayushert tana prison shi kuma yana kulle a gurin aikinsu..." a zabure mommy ta miƙe tsaye tana faɗin "a gaskiya bazan bar yarana su ƙara ƙwana acikin wannan halin ba, dole zanje na karɓe su, daman ai saboda ni akayi musu haka koh? toh yanzu zanje na karɓo kayana...". tana kaiwa nan tayi ficewarta daiden lokacin da aka shugo musu da kayan abinci, mommy ko tsaya kallon abincin batayi ba, suma haka suka biyo bayan ta malam Lawan yace "ku tsaya na kaiku da motata, kamata yayi mu fara zuwa dubo Junaid daga nan sai mu wuce prisoner..." haka kuwa akayi kai tsaye headquarters suka wuce, ★★★★★ Junaid kuwa yana ƙwance ga zazzaɓin da yake damunsa gaba ɗaya ya fita hayyacinsa, duk ya rarrame sakamakon rashin cin abinci domin idan ya tashi yaga abinci ba ci yakeyi ba saidai ya ɗan kurɓi lemo shikenam, sumar sajensa zuwa gemu duk yayi tsayi harta suman kansa saboda tsawon wata uku babu gyaran gashi balle ya rarrage sumar sai fuskar tayi fiyau, shima babu maraba da wanda yake zaman gidan prison, sai dai shi Junaid ana kawo masa abinci mai kyau ne sannan muhallin da yake shima mai kyau ne, fita ne kawai aka haramta masa, yana ƙwance ya lulluɓe kansa da mayafi kamar mai yin bacci, shi kaɗai yanata saƙe² aransa, tinda yake ba'a taɓa ɓata masa rai kamar na wannan karan ba, yana tunani aransa cewa "an raina mun wayo wallahi amma na yanke hukuncin koda sun nemi na dawo aiki wallahi bazan dawo ba, ni gurin da za'a rainani bana yadda na zauna a gurin, bansan kuma yaushe zasu buɗe mun ƙofa nayi tafiyata ba, waɗannan mutanen ba ƙaramin cutana sukayi ba dole naɗau fansan abunda suka mun, bazan ƙyalesu ba bansan a wani hali Yushert take ciki ba, ko sun kasheta ko tana gidan prison Allahu a'alamu, ya Allah ina neman agajinka! ya Allah ka temakeni banida wata mafita sai abunda ka zaɓa mun..." ya ƙarasa maganar yana kukan zuci.. bai ankara ba yaji ana ƙoƙarin buɗe ƙofar ɗakin, a zabure ya tashi zaune yana sauƙe numfashi daƙer, wani daga cikin sojojin ne ya shugo ya sanar masa cewa "ya fito ana son ganinsa..." yana kaiwa nan yayi ficewarsa a ruɗe Junaid yabi bayansa gudun kar a sake ƙarƙame shi, yana fita kuwa kayinsa ya fara juyawa wani irin hajijiya ne yake shirin ɗaukarsa, yana dafe da kayinsa, ganin bazai iya tafiya da kansa ba dasauri yasa hannu ya dafe jikin gini yana shirin kaiwa ƙasi, wasu sojoji ne su uku suka nufo kansa suna faɗin "lafiya kuwa Ogah Junaid, meyake faruwa ne?...". hannu suka kai suna shirin ɗago shi jin jikin yanda yaɗau masifar zafi yasa suka razana suka ce "wannan ai bashida lafiya ne, muyi saurin kaishi Office ɗin da General yake da iyayensa suna ciki.." a haka suka ɗaga shi yana jan ƙafa daƙer su kuma suna riƙe dashi, A lokacin dasu Mommy suka bayyano kowa saida ya tsorita da ganinta wasu kuma suka guggudu daƙer aka fahimtar dasu suka dawo hayyacinsu, Allah ya temaka General yana nan domin baya zaman nan, saida yazo ya shigar dasu Officer ɗinsa sannan yasa aka je buɗe Junaid, Bayan shigar dashi Officer mommy tana ganinsa tayi saurin miƙewa tsaye tana faɗin "subhanallahi meya samu yarona? me kuka masa?..." tayi saurin riƙe shi ta zaunar dashi, General ya dubi waɗanda suka kawo shi yace "daman bashida lafiya ne? shine baku sanar ba?.." girgiza kai suka yi tareda faɗin "wallahi bamu sani ba muma yanzu muka tarar dashi a wannan halin, dake ba wanda yake shiga cikin ɗakin sai wanda yake kaiwa abinci da zarar yayi bacci..." Jinjina kai General yayi tareda sunkuyar da kansa domin baisan mezai gaya musu ba, mommy durƙusawa tayi a gaban Junaid ta riƙo hannayensa tana kuka tareda faɗin "my son kayi haƙuri na aikata maka laifi, na tafi na barka ba'a son raina ba gashi na jefa ka a cikin mawuyancin hali ka gafarce ni my son...." Junaid idonsa a lumshe kamar a mafarki yake jiyo muryar Mommy, a hankali yake buɗe idonsa kansa a sama yana kallon ceilling yana daga zaune ya sunkuyo da kansa idanuwansa suka sauƙa akan mommy, a razane yakai hannunsa biyu yana murza eyes ɗinsa ko mafarki yake ganin a zahiri yake kallonta yasa ya miƙe da sauri yana zazzaro ido waje, Mommy itama tashi tayi tana cewa "ka ƙwantar da hankalinka my son nice momminka ban mutu ba..." ta ƙarasa maganar tana yowa kansa da gudu ya juya yana ƙoƙarin fita daga cikin officer sai ga Marshal shima ya shugo cikin rashin sani sukayi gwarai, Junaid baya ya yo yana riƙe da goshinsa shima marshal riƙe goshinsa yayi yana kallon Junaid tareda cewa "wannan wani irin ganganci ne haka..." shi kuwa Junaid bai wani damu da gwaran da sukayi ba tsabar hankalinsa yana kan mommy, malam Lawan ne ya nufo kanshi yana faɗin "kaga Junaid ka kwantar da hankalinka mahaifiyarka ce ta dawo gareka ba mutuwa tayi ba, ta samu agajin gaggawa ne yanzu kuwa ta samu sauƙi ta dawo..." ya ƙarasa maganar yana dafe da kafaɗarsa shi kuwa idonsa akan mommy baki na kakkarwa yace "are you sure? ka tabbatar mamana ne? bata mutu ba?..." Malam Lawan ya nuna sarki Raamud yace "kasan wancan mutumin?..." Junaid idonsa yakai kan sarki Raamud yana jinjina kai tareda faɗin "wannan shine Baban Yushert..." malam Lawan yace "tabbas shine kuma Baffanka, a lokacin da mahaifiyarka take neman agaji Narasimha ne yazo ya ɗauke ta sukayi mata magani..." cikin rashin fahimta Junaid yace "wanene Narasimha?.." malam Lawan girgiza kai yayi sannan yace "haba Junaid kodai duk firgicin ne ya hanaka tuna komai? na gaya maka komai akan su ai, sannan shi Narasimha shine malaminsu kuma likitansu kuma mai basu kariya..." sai a lokacin Junaid ya sauƙe nannauyar numfashi yace "wayyo Allah nah! na fahimta Allah na gode maka daka ceci mahaifiyata..." itama mommy kuka take tayo kansa tana faɗin "Junaid my son.." tasa hannu tana goge masa hawaye, cike da farin ciki Junaid yake kallon mommy yana dariya tareda zubar da hawaye yasa hannu ya rungumeta lokaci guda ya fashe da matsanancin kuka yana ƙiran sunan mommy, shi da mommy gaba ɗaya kuka suke yi babu mai rarrashin juna, Sarki Raamud ne ya zo yanda suke yasa hannu yana bubbugan bayan Junaid a hankali yana rarrashinsa, ɗagowa Junaid yayi yana faɗin "Mom meyasa zakiyi nisa dani, meyasa zakiyi tsawon watannin nan baki dawo gareni ba, na shiga damuwa sosai na rashin ganinki ga Yushert bansan a wani hali take ciki ba, shin sun kasheta ne ko tana raye, Mom Ina cikin damuwa..." Itama mommy kuka take tace "a'a my son Ayush tana raye, na dawo kenam bazan ƙara tafiya na barka ba my son, ka duba kaga yanda ka koma? duk ka fita hayyacinka akwai rashin kulawa a tattare dakai my son..." Junaid kallon yanda Marshal yake yayi sannan yace "Mom sun zalunce ni, suka kulleni tsawon wata uku banji iskar duniya ba, nabar aikin nan bazan ƙara zuwa aikin nan ba, gwara naita zama a gida amma babu ni babu aikin soja na ajiye, kuma daman ai sun koreni...." Mommy tana shafar fuskarsa tace "it's okay my Omomo duk yanda kace haka za'ayi tinda basu kula mun dakai yanda ya kamata ba...." General dake zaune yana sauraronsu ya katse su da cewa "a'ah Junaid bafa koranka akayi ba, an ɗan dakatar dakai ne kuma yanzu an dawo dakai bakin aikinka..." kafin ya iddasa maganar Junaid ya katse shi da cewar "impossible! bana juran wulaƙanci, da a wulaƙantani gwara na ajiye komai nawa sabida haka na ajiye aikina...." yana ƙarasa wa yaja hannun Mom yana faɗin "please Mom mu tafi am not feeling well..". ya jata sukayi waje, malam Lawan da sarki Raamud kuwa haƙuri suka tsaya bawa General kafin suma suka fice, duk ba wanda ya gane sarki Raamud sakamakon yayi shiga irin na hausawa, danƙararriyar gizna ne a jikinsa da babban gariya sai kuma hular daya ɗora akansa bayan rage tsayin sumar kansa dayayi, suna fita suka tarar da Junaid da Mommy a bayan seat suna zaune zaman jiransu, malam Lawan da sarki Raamud kuwa gaban motar suka shiga malam ne mai driving kai tsaye gida suka nufa, Junaid ganin gida ake shirin komawa yayi saurin dakatar dasu tareda faɗin "bazan koma gida ba saida Yushert ɗina..." murmushi malam yayi sannan yace "okay mu wuce prison kawai..." Mommy abun ya bata mamaki sosai tace "my son wai yaushe ƙullaliyar soyayya ta shiga tsakaninku har haka ne?...". kawar da kai Junaid yayi yace "Ni ina fushi dake mommy tinda har zaki ɗaura mun Aure ba tareda sanina ba..." Murmushi mommy tayi sannan tace "Hmmm! a lokacin wahalar dani zakuyi shiyasa ban sanar muku ba amma tinda yanzu kun gane da kanku shikenam..." suna cikin hirar su har suka isa gidan prisoner, wani ne daga cikin security ya shugo dasu har cikin prison aka kaisu wajen da zasu zauna, shi kuwa ya tafi ƙira musu Ayush... Ayushert tana ƙwance a ɗakinsu sakamakon ciwon cikin dake damunta, ga yanda cikinta yaketa motsi shi kaɗai ita kuma Hafizat taje tana musu wanki, wata mata ce christal ta shugo cikin ɗakin ganin Ayush a cikin wannan halin ne yasa tazo gabanta da sauri ta tsuguna tana faɗin "sorry kinji koh, cikinki na miki ciwo ko sorry, tashi maza kinji..." Ayush daƙer ta iya tashi saida christal ta temaka mata ta kuma cewa "cikin ki yanzu wata nawa ne?.." Ayush tana kallonta cikin sanyayyar murya tace "jiya likita tazo dubani ta ce yanzu ya shiga wata takwas ne..." Joy tace "wow halalluya kin kusan haihuwa, yanzu aka sanar mun cewa kinyi baƙi suna can guess place...". Ayush zaro ido tayi tana dafe da ƙirjinta tace "daga kotu ko? sun zo dubani ne da zaran na haihu su ratayeni.." Joy tayi murmushi tace "ki ƙwantar da hankalinki babu abunda za'a miki, wannan baƙin bana kotu bane tashi muje ko.." ta riƙe hannun Ayush ta tallafa mata ta tashi daƙer take tafiya tsabar girman cikin, Bayan isar su guess su Mommy suna zazzaune akan kujeru, Junaid ne ya fara ganin Ayush da sauri ya miƙe ya nufi wajenta yace "Yushert..." rungumarta yayi tare da faɗin "nayi kewar ki Yushert, i missed you my Yushert..". itama rungumarsa tayi sosai tare da fashewa da kuka ba tare da tace komai ba, su Mommy suma miƙewa tsaye sukayi ko wannensu da damuwa a fuskarsu ganin Ayush a cikin wannan halin, shi kam sarki Raamud yafi kowa shiga damuwa domin har da ƙwallarsa yana maganar zuci "wai yau Ɓingel ce a prison? ban taɓa tunanin yarinyata zata shiga cikin wannan halin ba, innalillahi wa inna ilaihi raju'un..." Junaid ne yasa hannu ya raba jikinsa dana Ayush yana nuna su Mommy tareda cewa "Yushert kin gane waɗannan?..." Ayush kallonsu take ɗaya bayan ɗaya tadai gane malam Lawan amma sarki Raamud sam bata gane shi ba, still idonta ta sauƙar akan Mommy sai murmushi take tayi amma a cikin zuciyarta ta damu sosai ganin Ayush a prison... Zaro manya-manyan idanuwanta tayi sosai kamar zasu faɗo ƙasi tasa hannu ta ƙanƙame Junaid da ƙarfi, leɓɓen bakinta har rawa suke haƙwaranta na dukan na juna sam ta kasa furta komai sai jikinta dake kakkarwa idonta kuwa akan mommy, Itama mommy zaro ido tayi waje cike da mamaki take kallon tumbin cikin Ayush, tin zuwanta bata lura ba sai yanzu, cikin ɗaga murya mommy tace "Junaiddd!! yaushe ka bata ciki? har ta kusan haihuwa innalillahi..." haka ta baza idanu ta kalli Junaid sannan ta maida idonta kan cikin Ayush still ta kuma kallon Junaid haka ta rinƙa yawo da eyes ɗinta, Junaid kuwa tsabar kunya kawai da kansa gefe yayi ga mutane a wajen waɗanda aka kawo musu visit, yana jin yanda Ayush take ta bubbugansa tana so tayi masa magana amma yaƙi juyowa, Ita kuwa Mommy sai cewa take "Junaid! Ayush!! wai yaushe kukayi cikin nan ne kam ku mun bayani mana, amma bayan tafiyata kukayi wannan cikin koh? Alhamdulillah Allah yaga zuciyata gwara dana ɗaura muku Aure bansani ba ashe a matse kuke..." haka mommy take ta wannan surutan gashi ba'a hankali take magana ba kowa sai jiyota yake, waɗanda suke gefen can duk hankulansu ya dawo kan su Mommy, Malam Lawan da sarki Raamud kam ficewa sukayi suka nufi waje saboda mutanen dake wajen, Junaid kamar ya nitse ƙasi cikin takaici yace "Oh my god haba Mommy sai kace wata ƙaramar yarinya..." sake baki mommy tayi tana kallonsa tace "ahhh ku kam ai kun girma, tabbas na yarda kun girma kun wuce ace muku yara gashi har zaku haifi yara ai kun zama manya tinda har kuka aikata abun manya..." kamar zai rausa ihu yace "eh ai ba bad pregnant bane..." Mommy tace "eh ai nasani tinda ni da kaina nasa akayi muku Aure, ikon Allah kenam gashi har ka samu damar ɗura mata ciki...." Junaid hararar Mommy kawai yake kamar zaiyi kuka ita kuma Ayush sai jijjiga shi take juyowa yayi yana faɗin "wai ke ɗin menene kam?.." cikin kakkarwar murya tace "Mommy ce ko Fatalwa?..." yace "Da fatalwa ce zaki jita tana wannan surutai ne, ni sake ni! my headache ta dawo gaba ɗaya ta ɓata mun raii..." haka ya zamar da hannunsa daga jikin Ayush yabar wajen yana gunaguni... Mommy ce tayo kan Ayush tana faɗin "Oyoyooo my Ayushertttt..." ta rungumeta sosai a jikinta, Ita kuwa Ayush tinin ta ƙafe a wajen tsabar tsoro saida tasau fitsari a jikinta tana daga tsaye..... *ASSALAMU ALAIKUM ƳAN UWANA BARKA DA WANNAN LOKACIN, INA MAI MIƘA GODIYATA A GAREKU NAJI DAƊIN ADDU'O'INKU AKAN ƊAN UWANA WANDA YA RIGAMU GIDAN GASKIYA🙏🙏🙏* *BAZAN TAƁA MANTAWA DA WANNAN HALACCI DA KUKA MUN BA INA GODIYA SOSAI...* *YAU DAI NA DAURE NAYI MUKU UPDATE, NACE BARI NA SAMU NA KAMMALA MUKU KAR NIMA NA MUTU DA HAKKIN KU AKAINA, INA ROƘON ALLAH DA YA ARA MUN RAYUWA HAR NA KAMMALA MUKU LITTAFIN NAN SAKAMAKON ƊARA RANKU DA KUKAYI AKANSA INA MAI JINJINA MUKU MASOYANA NA FILI DANA ƁOYE🙏🙏🙏*... 𝑡𝑦𝑝𝑖𝑛𝑔✍️ 𝗠𝗔𝗧𝗔𝗥 𝗗𝗔𝗠𝗨𝗦𝗔 the wife of a tiger🐅🐅🐅🐅 𝙼𝚊𝚕𝚕𝚊𝚔𝚒𝚗 𝙰𝚜𝚖𝚎𝚎𝚝𝚊𝚑 ✍️✍️ 𝙿𝚊𝚒𝚍 𝚋𝚘𝚘𝚔 𝚌𝚊𝚕𝚕 𝚘𝚛 𝚠𝚑𝚊𝚝𝚜𝙰𝚙𝚙 09065443871 *💫💫{{N W A}}💫💫* Book two C̶h̶a̶p̶t̶e̶r̶ 59 ➡️ 60 Mommy tana rungume da Ayush bata san lokacin data suma ba, sai nauyinta data ji yayi over ga tilin tumbi Mommy har tana shirin faɗuwa ta tattaro iya ƙarfinta a hankali ta kai Ayush ƙasa saboda bazata iya riƙeta a tsaye ba, zaro ido waje mommy tayi tareda faɗin "nashiga uku me kuma ya faru dake Ayushert?..." tattaɓa fuskarta ta soma yi amma shuru Ayush ko motsi, fashe wa da kuka mommy tayi tana neman agaji ƙiran mutanen wajen ta soma yi, duk aka rufu akanta amma an rasa wanda zai taɓata suna cikin wannan halin saiga su Junaid da malam Lawan sun shugo da sauri sakamakon sanar musu da akayi a waje, a ruɗe Junaid yasa hannu ya ɗagota yayi hanyar waje da ita, masu tsaron prison ne suka bi bayansa suna son dakatar dashi, har zai buɗe murfin motar suka dakatar da shi da faɗin "ba'a bada umarni a fitar da mai laifi a cikin wannan prison ba, wannan kuskure ne..." Junaid ya juyo yana kallonsu ɗaya bayan ɗaya sannan yace "baku ga a halin da take ciki bane?..." suka ce duk da haka sai an bada umarni tukun, su Mommy ne suma suka ƙaraso wajen da sauri cikin damuwa take faɗin "dan Allah kuyi haƙuri mu kaita asibiti idan baku yadda damu ba saiku biyo mu muje tareda.." wani ne daga cikinsu yace "okay amma kafin nan sai kun bada information nakun.." a lokacin suka bada sannan suka shiga motar kai tsaye hospital suka nufa da ita tareda security guda biyu... Ranar a hospital suka kwana, iya malam Lawan ne kawai ya koma gida amma Junaid da Mommy da kuma sarki Raamud duk a asibiti suka wayi gari, a lokacin da Ayush ta farfaɗo su Mommy basa nan sunje shigar da report akan Ayush na anason fitar da ita daga prison, an karɓi ƙorafinsu amma sai an sake zama a kotu an nunawa duniya cewar Doctor Fateema ba mutuwa tayi ba sannan kuma a wanke Ayush a kotu.... Bayan farfaɗowarta Junaid kawai ta tarar a kusa da ita yana zaune ya zuba mata ido, itama kallonsa take a hankali take motsi da leɓɓenta tace " mafarki nayi ko? nasan mommy bazata taɓa dawowa ba, na tamka babban kuskure a rayuwata, da hannuna na kashe mommy nima rayuwata batada wani amfani..." kuka ne yaci ranta sosai dasauri Junaid yasa hannu yana rufe mata baki tareda girgiza mata kai yace "kar na sake jin wannan batun, mommy bata mutu ba ta samu tsira ne.." hannu tasa ta zamar masa hannunsa dake kan bakinta tana ƙoƙarin ɗagowa zaune daƙer har saida ya tallafa mata tana kallonsa cike da mamaki take cewa "tayaya hakan zata faru? taya zakace mommy bata mutu ba shin ɓacewa tayi ne ko meye?..." murmushi yayi sannan yace " Narasimha..." da sauri Ayush ta ɗago tana kallonsa baki na kakkarwa ta maimaita sunan "Narasimha?..." shima idonsa akanta yace "yes ko kin sanshi ne?.." idonta akansa ko ƙibtawa batayi ta jinjina a cikin ranta take cewa "na sanshi shine yayi mun magani lokacin da na cire zobe a jikin cibiyata, kenam shine yazo ya ɗauketa..." tana cikin wannan tunanin taji Junaid yana faɗin "tunanin mai kike yi ko kin sanshi ne?..." a ruɗe tace "kenam masarauta aka kaita ta ɗebi tsawon watannin nan?.." jinjina kai Junaid yayi yana kallonta, a lokacin jikinta yayi sanyi kamar wacce aka zuba masa ruwan sanyi kai a ƙasi, daiden lokacin da su Mommy suka dawo da wasu takardu a hannunta, Ayush tana ganinsu tayi saurin ƙwanciya ta kifa kanta acikin filo domin a halin yanzu bazata iya haɗa ido da mommy ba, mommy zama tayi a bakin gadon ta ɗora hannunta akanta tana faɗin "ya hakane Ayushert ki ɗago mata na ganki nayi kewar ki, Alhamdulillah da Allah yasa kika farfaɗo lafiya duk da nasan saboda ni kika suma, kiyi haƙuri kinji ni ɗin ce mommy ba wata ba ...." Ayush tana jinta amma ta kasa ɗagowa, har saida sarki Raamud ya matso kusa da ita ya kawo kansa saitin kunnenta yana mata raɗa da cewa "Ɓingel karki nuna rashin wayo ki tashi ki nemi yafiyar ta akan abinda kika aikata mata, zata ji daɗi domin in baki kasheta bama kin tafka mata babban asara...." yana ɗagowa itama ta tashi tareda fashewa da matsanancin kuka ta sauƙa daga kan gadon ta ɗayan ɓangaren ta zagayo tareda durƙusawa ƙasi agaban mommy tana kuka tana faɗin "mommy dan Allah kiyi haƙuri akan abunda na aikata miki wallahi nima nasan banyi miki adalci ba, haƙiƙa nayi miki butulci a rayuwa domin ko mahaifiyata bata nuna mun kulawar da kika nuna mun ba, kin nuna mun soyayyar gaskiya tamkar uwar da take matuƙar son ɗiyarta, ..." kuka ne yaci ranta sosai har ta kasa ƙarisa maganar, itama mommy kuka take tana kallon Ayush cikin tausayawa tasa hannu ta ɗagota tareda rungumarta a jiki tace "kiyi shuru my daughter banson jin kukan ki, wallahi baki mun komai ba abunda kika aikata ko kaɗan banji tsanarki ba domin na ɗaukeki tamkar ƴar dana haifa a cikina, karfa ki manta ciki na fa kika ƙi sannan kika fito a cikin ƴar uwa Bara'at, saboda haka ki ƙwantar da hankalinki komai yazo ƙarshe, insha Allahu daga yau baza ki sake kwanan prison ba, my daughter na yafe miki duniya da lahira..." Ayush itama rungumar Mommy tayi tana rera kuka mai ratsa zuciya, sun shafi mintuna a haka kafin mommy ta samu nasarar rarrashinta sannan tayi mata albishir da cewa daga nan ba komawa prison, ba ƙaramin farin ciki Ayush tayi ba tana cikin murna lokaci guda ta maida fuskarta kalar tausayi a shagwaɓe tace "Mommy.." kallonta mommy take cikin kulawa ta amsa mata da cewa "na'am ƴar mommy ya akayi ne?.." tana zubda hawaye tace "missing someone very close to my heart..." Junaid cikin rashin fahimta yake kallonta fuska a ɗaure, sarki Raamud shima yana zaune akan kujera baiyi tunanin komai ba ya ɗauka ta tuno da mahaifiyarta ne, shima ba ƙaramin tausayawa ɗiyarsa yake ba amma saidai ta wani ɓangare hankalinsa a ƙwance yake tinda har Allah ya haɗasu da mommy mai ƙyakykyawar zuciya. Mommy kallon Ayush tayi sannan ta kalli yanda Junaid yake a zaune still ta maido da eyes ɗinta kanta tareda faɗin "amma waye wannan wanda kika yi missing ɗinsa haka?..." girgiza kai Ayush tayi sannan tace "ba namiji ba, mace ce na haɗu da ita ne a prison, yarinya ce ƙarama tana buƙatar temako..." Junaid ne ya sauƙe wata nannauyar numfashi a bayyane yace "thank God..." Daga Ayush har mommy tsaya kallonsa suka yi daga bisani mommy tace "lafiya kuwa Junaid?...". ɗaga musu hannu yayi tareda faɗin "no ku cigaba da hirarku..." daiden lokacin da Malam Lawan ya shugo da sallama a bakinsa suka gaggaisa sannan ya nemi guri ya zauna, ya sanar musu cewa "ranar 10 ga watan January za'a koma kotu koh?..". Mommy tace "eh ganan takardar ma amma daga nan gida zamu wuce da Ayush..." Ayush dasauri ta katse mommy da cewa "dan girman Allah mommy ku temaki Hafiza tana cikin mawuyancin hali, gashi na baro cikin prison ba tareda ta saniba saidai ta nemeni ta rasa, yarinyar ta shiga raina du Da du mah shekarar ta 18 a duniya..." Mommy zaro ido waje tayi tana maimaita kalmar "18 years old? amma ya akayi ta shiga prison a wannan ƙarancin shekarun natan?..." anan Ayush ta kwashe komai dangane da yarinyar ta gaya musu, ba ƙaramin tausaya mata sukayi ba, mommy tace "insha Allahu baza mu barta ta ƙare rayuwarta a cikin prisoner ba, zan tsaya mata tsayin daka Allah Sarki baiwar Allah, saboda iyayenta basu da kuɗi shine akayi amfani da dukiya domin aga ta tagayyara, insha Allahu hakan bazata faru ba, nima zan zubar da ruwan kuɗi domin naga ta fito ta cigaba da rayuwarta cikin aminci..." kowa saida ya tofa albarkacin bakinsa, Ayush ba ƙaramin farin ciki tayi ba jin Hafiza zata fito daga maƙarƙama.... anan suka shiga hirar su na rayuwa, mommy kaf saida ta ƙwashe rayuwar da tayi a cikin masarauta ta sanar musu ta ƙare maganar da cewa "ai wallahi banso barin masarauta ba, kawai nazo ne saboda yarana amma banda haka babu abunda zai dawo dani Nigeria..." Sarki Raamud yace "Ni ai bazan iya zaman wannan ƙasar takun ba, duk zafi yabi ya ishi mutum ga ƙura da rana bazan iyaba, yanzu idan na tashi komawa tare zamu koma ai..." ya ƙarisa maganar yana kallon mommy, juyowa mommy tayi tana kallonsa cikin gatsine tace "waa? saidai gaba ɗayan mu zamu tafi tare da su Junaid, yauwa ga ƙafata ga ƙafarsu domin bazan iya rayuwa ba tareda su ba..." Malam Lawan ba abunda yake musu inba dariya ba, Ayush itama dariya take tace "ai masarauta ba ƙaramin haɗuwa yayi ba, Ni tinda nake ban taɓa ganin tsararren masarauta haɗaɗɗe kamar masarautar mu ba ga girma, yanzu iya Yaya Junaid da malam Lawan ne kawai basu shiga masarauta baa..." Zaro ido Junaid yayi yana kallonta yace "waya gaya miki?..." Mommy tace "kin manta yaƙin da suka je neh?..." Ayush tace "wooo hakane fah ashe! Yaya Junaid ya kaga tsaruwar masarauta?..." juyar da kai gefe yayi domin shi Junaid har yanzu akwai wannan miskilancin nasan, shi baya son irin wannan doguwar hirar.. Sarki Raamud yana kallon Ayush yace "shima Malam Lawan ai ɗan cikin masarauta ne, a cikin masarauta aka haife shi kuma ya taso a cikinta..." Ba Ayush ba hatta Junaid da Mommy abun ya ɗaure musu kai, gwara ita mommy sun sanar mata a baya amma har yanzu tana mamakin faruwar hakan, Ayush cikin rashin fahimta tace "tayaya kenam? nifa malam Lawan a daji na sanshi ya zauna damu ni da mahaifiyata daga baya ya tafi domin shine ya koya mun karatun Alkur'ani da wasu abubuwa na addinin musulunci..." Shima Junaid abun ya bashi mamaki domin malam Lawan bai taɓa sanar musu haka ba, kuma shine ya bashi labarin rayuwar Ayush a daji ita da mahaifiyarta amma bai sanar masa yayi rayuwa dasu ba... Malam Lawan ne ya kalli Junaid da murmushi a fuskarsa yace "yadai Ogah Junaid kaji abu kamar daga sama koh?..." shima Junaid ɗin shi yake kallo cikin rashin fahimta. Malam Lawan yace "kar ku damu yanzu zan warware muku komai, zaku san ko ni wanene a yanzu, Da farko dai sunana Artaff Zaidullah Hussein Ni ɗa ne agurin Sarki Zaid mahaifin Raamud da Máahmud ni ƙaninsu ne amma mahaifiyar mu ba ɗaya bane, su alokacin da mahaifiyarsu ta haifesu ƴan biyu Allah ya karɓi rayuwarsu, kasancewar masarautar ba'ason sarki ya zauna babu mata yasa aka Aura masa ƴar Sarkin ƙasar Iran, wato mahaifiyata Gimbiya Maryama! tinda aka haifeni Máahmud yake jana a jikinsa har na fara wayo a yayinda shi kuma Raamud yake ƙina, ko inuwarsa naje yakan hantareni haɗi da duka, koda mahaifiyata baya son zuwa yanda take daga waran mahaifin mu babu waran da yake zuwa, hakan yasa ya fara jin haushi ɗan uwansa saboda ni, haka rayuwa take tafiya yanda ya kamata har muka mallaki hankalin kan mu a lokacin ne ƙiyayya ta ƙullu a tsakanina da Raamud baya ƙaunar ganina saboda wai kar a bani mulkin masarauta, Allah Sarki ga yayuna waɗanda suka rigani shan iskar duniya taya za'a ban mulki kuma, a lokacin da mahaifin mu yake shirin sauƙa ya tara mutane ya sanar cewa zai bawa Yayan mu wato Máahmud mulkin masarauta anan Raamud ya maida ƙiyayyata zuwa kan ɗan uwansa Máahmud, har yayi sanadiyar da aka kai farmaki cikin masarautar, a ranar ni kuma da mahaifiyata munje ƙasar Iran gano mahaifinta yana ƙwance ba lafiya ciwon ajali ya riskoshi, a ranar da mahaifin mahaifiyata ya rasu a ranar saƙo ya risko mu kan cewar an kai farmaki cikin masarautar mu har anyi nasarar kashe mahaifin mu sarki Zaid, Máahmud kuma an ɓatar dashi ƙwata-ƙwata, naji ba daɗi sam na kuma yi rashin mahaifina da kuma kakana na waran uwata, Mahaifiyata kuwa tinda ta suma jin mahaifinta ya rasu ga kuma saƙon mijinta shima ya rasu ga kuma Máahmud wanda ta sashi a ranta shima baya nan daga nan bata ƙara farfaɗowa ba sai bayan watanni uku nan ma saida aka dage da addu'o'i da maganganuwan Musulunci tukun Allah ya bamu nasarar ceton ta amma har zuwa wannan lokacin tana nan a ƙasar Iran ko magana bata iya yi saboda damuwar dake ranta, tana dai cin abinci tana komai amma bata cewa komai sannan ba sosai take iya gane mutum ba sakamakon hawan jinin da take fama dashi amma tana raye har yanzu, wasu lokuta nakan je na dubota, tare muka cigaba da zama da mahaifiyata a ƙasar Iran bamu sake komawa ƙasar california ba cikin masarauta, a Iran na cigaba da karatuna har nayi boko da Arabic, amma nafi zurfafa karatuna akan musulunci har Allah yasa na zamo babban malami a ƙasar Iran, amma duk hankalina yana kan binciken yanda zanyi na samo ɗan uwana Máahmud, har Allah ya bani sa'a na samo shi, ya kuma ɓoyeni a gurin matarsa wato Doctor Fateema ya nuna mata cewa ni Abokinsa ne, muka zauna a haka amma bansan dalilinsa nayin haka ba, har Allah ya kawo Bara'atu cikin rayuwarsa ina ganinta nasan akwai ƙullaliyar al'amari domin Ni Allah ya bani wani irin baiwa na saurin gano mutum, ni ba matsafi bane amma ina iya gano komai akan mutum kuma duk wasu bayanai na Raamud ina sanin su domin shima bazan iya fita daga cikin rayuwarsa ba, duk wasu ƙalubalen da yake faruwa da Raamud na sani, domin shi ya shiga jikin Bara'at ta hanyar tsafi ya Aureta ya kuma shiga jikin Máahmud har yayi sanadiyar mutuwarsa ta dalilin cikin Raamud dake cikin Bara'at, wanda a lokacin mun shirya ni da Mahmud akan cewar zamu sanar da matarsa gaskiyar lamari akan Máahmud da kuma ni kaina sai dai Allah bai yadda ba... A lokacin da Bara'at ta koma jeji da zama nabita naje na zauna dasu saboda nasan ba laifinta bane na koyar dasu abubuwanda basu saniba, nayi hakane saboda bazan taɓa barin Ahalina su tagayyara ba, koba komai Bara'at da ɗiyarta sun zamo jinin mu bazan gujesu ba, kuma shi kansa Raamud bazan taɓa ƙinsa ba duk da ƙiyayyar da yake nuna mun a baya, naji daɗi yanzu da aka sanar mun cewa Masarautar mu ta gyaru, insha Allahu masarautar mu bazai taɓa barin hannun mu ba saidai idan mun ƙare gaba ɗayan mu....." Daga nan yaja ajiyar zuciya a yayin da hawaye suka wanke masa fuska... Cikin macewar jiki sarki Raamud yakai hannu ya dafa kafaɗar malam Lawan sannan yace "Artaf kayi haƙuri nasan na aikata babban kuskure a rayuwata, nima kawai ina rayuwa ne amma bana jin daɗinta, na tsani kaina! idan na tuna cewa nine nayi sanadiyar mutuwar mahaifin mu sai naji kamar na rataye kaina, idan na tuna cewa ni nayi sanadiyar mutuwar ɗan uwana sai naji kamar nasha guba na kashe kaina, idan na tuna cewar ni nayi sanadiyar tarwatsewar rayuwar matata da kuma ɗiyata sai naji kamar nake gaban trailer ta murƙusheni, idan na tuna cewa ni nayi sanadiyar wargaza rayuwar Junaid da kuma sanya mahaifiyarsa cikin damuwa sai naji kamar na nasa wuta ajikina, idan na tuna cewar ni nayi sanadiyar jefa matar mahaifina cikin jinya sai naji kamar na datsawa kaina wuƙa amma idan na tuna cewa Allahu gafurur Raheem sai naji nutsuwa a raina, amma kuma idan na tuna cewa Allah baya shiga tsakanin bawa da bawa saidai idan wanda ka zalunta ya yafe maka sai naji kamar naita ihu, idan har haka ne aina zan samo Babana ya yafe mun? Aina zan samo Ɗan uwana ya yafe mun?..." kuka ne ya ƙwato masa mai cin rai, da ƙarfi yake wannan kukan, shima Artaff rungumar ɗan uwansa yayi yana tayashi kukan, Gaba ɗaya jikin mommy ne yayi sanyi babu ƙarfi ko kaɗan, Junaid kansa a sunkuye ko ɗagowa ya kasayi sakamakon hawayen da suka wanke masa fuska, Ayush itama jin yanda Mahaifinta yake kuka yasa itama ta fashe da matsanancin kuka duk idanuwanta sunyi jawur kana ganinta kasan ba tin yanzu ta fara kukan ba, Artaf yana kuka ya ƙarasa musu labarin da cewa "Matata ba ƴar nan ƙasar bace, ƴar ƙasar Iran ce ƴar ƙanwar mahaifiyata aka Aura mun, muna zaman mu acan na ɗaukota muka dawo nan Nigeria saboda iyalan Ƴan uwana wato Máahmud da Ɗansa da kuma Matar Raamud da Ɗiyarsa, saboda ku na dawo Nigeria da zama sakamakon nayi Alƙawari wa kaina cewa zan kula daku, zan riƙe ku Amana, bazan bari ku tozarta ba, duk rintsi duk wuya ina tareda ku, shi Raamud ban damuba saboda nasan Amanar Mahaifinmu yana tareda dashi wato Narasimha...." anan ya ƙara fashewa da kuka.... Sarki Raamud shima ƙara volume kukan yayi saboda abunda ya wuce a baya ba ƙaramin tayar masa da hankali yake ba, Ga muryar Ayush itama yanda take ta kuka bugu da ƙari ma ta tuno da mahaifiyarta, Mommy jin yanda suke ta kuka ne yasa itama ta fashe da kuka ta tuno da mijinta, Junaid jin yanda suka hargutsa cikin ɗakin da kuka babu mai rarrashin kowa yasa ya tashi yabar ɗakin domin a halin yanzu bashida sukunin da zai iya rarrashinsu, kuma acikinsu baisan wazai fara rarrashi ba, shin Uncle Artaff zai rarrasa ne ko kuma Sarki Raamud ko kuma Ayush ko kuma mommy wacce ta fara yanzu?.." haka yana ji yana gani ya barsu ya fice abunsa.... *TAPAH ASHE ƳAƳAN SARKI ZAID SU UKU NE MUKA MANTA DA ƊAYA ACIKINSU, WATO ARTAFF MALAM LAWAN KENAM* *JINI BAYA ƁUYA SAI WANDA BAI LURA BA, SHIMA ARTAFF BAMAI GANINSA YACE ƊAN NIGERIA NE, HABA BIRI YAYI KAMA DA MUTUM* *MÁAHMUD ZAIDULLAH HUSSEIN* *RAAMUD ZAIDULLAH HUSSEIN* *ARTAFF ZAIDULLAH HUSSEIN* *And their kids* *JUNAID_KHAN MÁAHMUD ZAID* *MAYUSHERT RAAMUD ZAID* *with two kids from Artaff* *Zaid Artaff Zaid* *Maryam Artaff Zaid* *Sumaiyah Artaff Zaid* Sumaiya mahaifiyar su Sarki Raamud kenam yayi mata mai suna da mahaifiyarsa da kuma mahaifinsa..... 𝑡𝑦𝑝𝑖𝑛𝑔✍️ 𝗠𝗔𝗧𝗔𝗥 𝗗𝗔𝗠𝗨𝗦𝗔 the wife of a tiger🐅🐅🐅🐅 𝙼𝚊𝚕𝚕𝚊𝚔𝚒𝚗 𝙰𝚜𝚖𝚎𝚎𝚝𝚊𝚑 ✍️✍️ 𝙿𝚊𝚒𝚍 𝚋𝚘𝚘𝚔 𝚌𝚊𝚕𝚕 𝚘𝚛 𝚠𝚑𝚊𝚝𝚜𝙰𝚙𝚙 09065443871 *💫💫{{N W A}}💫💫* Book two C̶h̶a̶p̶t̶e̶r̶ 61 to 65 Bayan fitar Junaid da minti talatin sai gashi ya shugo hannunsa riƙe da tray na Apple har guda goma, kowanne saida yaje gabansa tukun ya bashi Apple, kowa acikinsu yaci amma banda Ayush wacce ta ɓare baki tana kuka kuma taƙi karɓan Apple cikin dabara Junaid ya ɗauki gudan Apple ya cusa mata a cikin bakinta yana mata alamar tayi shuru da yatsansa, itama shuru tayi tana ajiyar zuciya tareda gutsiran Apple, A wannan lokacin dai babu wanda yayi wa kowa magana da haka aka sallame su suka koma gida, Gidan da Junaid yake anan suka sauƙa saidai kowa an ware masa part ɗinsa, Mommy da ɓangaren ta daban, shima Sarki Raamud da nasa ɓangaren, sai part ɗin su Junaid da Ayush dake can saman Upstairs.... Bayan an gabatar da Ayush a kotu tareda wanke duk laifukan da ake zarginta da aikatawa a lokacin akayi nasarar fitar da Hafiza daga prison, Amma Mommy ba ƙaramin ɓatar da kuɗi tayi ba a wannan case na yarinyar nan, Iyayenta sunyi matuƙar farin ciki sosai da kuma yin nadamar Aurar da ɗiyarsu a gurin da ba'a ƙaunarta, haka Hafiza ta cigaba da zama agurin su Mommy bayan iyayenta sun koma garin Kano, Ogah Junaid shi da kansa yasa Hafzat a makarantar sacondary, Hafzat ba ƙaramin farin ciki tayi ba kasancewarta dasu Mommy ga suna bata kulawa yanda ya kamata duk abunda ta nema bata rasa shi duk da tana da filako sosai dake bafulatana ce, Yau Saturday ranar weekend Hafzat tana zaune a babban falo ta ƙurawa plasman ido ana showing indian film mai kyan gaske, ita kaɗai sai murmushi take ganin an nuno masoya biyu sunata shan love, har Ayush ta sauƙo falo Hafzat bata sani ba, Ayush tayi sallama shuru har ta komo tana gyaran murya amma ko motsi Hafzat bata yi ba, saida Ayush ta ɗauki remote ta chanza Film ɗin tukun ta waiwayo da sauri tana son ganin wanda ya canza mata, ganin Ayush a tsaye tasha doguwar riga da gyalen kayan tayi kyau sosai tasau murmushi tana faɗin "laaa Aunty Ayusher kece?..." Ayush girgiza kai tayi tana cewa "uhmm uhmm bani bace ke ce..." Hafzat ɗan turo baki tayi sannan tace "wallahi Aunty Ayusher bansan kin shugo ba, yanzun ina zakije na ganki da shirinki har haka?.." "ina zaki san na shugo kina kallon yanda ake romance, mommy tana part ɗinta ne?.." Hafzat tace "a'ah bata dawo daga hospital ba...". "Okay Abbana pah?.." Ayush tayi maganar tana nuna part ɗinshi da yatsa.. "wallahi bansani ba ko yana nan, amma naga shiɗin baya fita ko ina ai.." a cewar Hafzat.. Ayush tace "Hmmm! Abbana kuwa ina ya sani a Nigeria, bari naje na dubo shi, daga nan zan wuce hospital ne zanyo scan, ita kuwa Mommy nasan zamu haɗu acan..." Hafzat tace "toh Aunty a dawo lafiya" Kai tsaye part ɗin sarki Raamud ta nufa wanda yake da tazara sosai da falon, tacan cikin falonsa akwai hanyar fita waje, tana shiga falon ta tarar baya nan, daga nan ta wuce bed room ɗinsa a bakin ƙofa ta tsaya tana knocking a hankali, daga ciki akayi magana tareda cewa "waye?" Cikin sassanyar murya tace "Ni ce Abba..." "Ok shugo mana" daga ciki ya bada permission.. tura ƙofar tayi tareda sallama ta shige ciki da murmushi a fuskarta ganinsa akan sallaya da Alkur'ani mai girma a gabansa, zuwa tayi ta zauna a kusa dashi tace "ina kwana Abbana.." shima da murmushi a fuskarsa ya amsa mata cike da zolaya yace "Ɓingel Maman twins.." zaro ido tayi tareda toshe bakinta da hannayenta biyu ciki² take faɗin "haba dai Abba twins kuma, a'a ni da guda ɗaya ɗaya zan haifa saboda samun sauƙi na..." Dariya yayi tareda girgiza kansa idonsa akan Kur'ani yana shirin rufe shi yace "Ɓingel kenam har yanzu dai bakiyi wayo ba, yanzun sai ina?..." ɗan turo baki tayi cikin shagwaɓa tace "hospital zanje.." yace "a'a toh tashi kije kar lokaci ya ƙure miki, nima yanzu wanka nake son shiga.." tashi tayi tareda cewa "toh Abbana saina dawo" ★★★★★★ Ata ɓangaren Lailah kuwa ta samu sauƙi sosai domin yanzu tana cikin hayyacinta amma saidai bata iya gane kowa, yanzu waɗanda ta sani sun dawo mata tamkar sababbin fuskoki, amma zata zauna tayi hira da mutum, a yanzu dai iya Doctor Mansur kawai ta sani domin a koda yaushe shine a jikinta, koda wasa bai taɓa gajiyawa da ɗawainiya da ita ba, kuma wani ƙakƙarfar alaƙa ne ya shiga tsakaninsu wanda idan Lailah bata ga Doctor Mansur ba hankalinta tashi yake, shi kuwa baya ƙaunar tashin hankalinta shiyasa baya barin yanda take saidai idan tana bacci, Doctor Mansur yana iya ƙoƙarinsa akan Lailah tasan tana da ƴan uwa musamman Doctor Hasheem da yake prison, koda yaushe yakan bata labarinsa har tasa a ranta cewa tana da Yayanta a prison kuma ana yawan nuna mata photonsa hakan yasa take muradin ganinsa, yau ma kamar kullum tana zaune a saman gado shi kuma Doctor Mansur yana kusa da ita a zaune a bakin gado yana ɓare mata wasu maganinnuwa da bottle na ruwa akan table, ta ƙura masa ido sai kallonsa take ko ƙibtawa bata yi tana motsa baki a hankali cikin sassanyar murya tace "JAAN..." ɗagowa yayi da kyawawan idanuwansa yana kallon cikin taurarin eyes ɗinta da murmushi a fuskarsa ya amsa mata da "Na'am Baby..." cikin kasalalliyar murya tace "kai kyakkyawa ne.." suna cikin kallon juna ya ƙibta mata ido ɗaya tareda kai hannunsa saitin bakinta yace "HAAAA buɗe bakin ki kisha magani.." a hankali ta buɗe ya saka mata su tareda kafa mata bakin gorar ruwa, haka take shan ruwan tana lumshe ido, shi kuwa hakan ba ƙaramin burgeshi take yi ba, shima haka ya ƙura mata ido da kyawawan sex eyes ɗinsa, a cikin zuciyarsa kuwa cewa yake "Masha Allah! tabarakallah Godiya ta tabbata ga sarkin halittun duniya wanda ya halitta mun wannan kyakkyawar ɗawisu, Yaa Allah ka mallaka mun wannan halittar ka a mazannin matata ta Aure..." duk Abunda yake so a game da mace gaba ɗaya Lailah ta tara su, Lailah she is a black beauty, amma saidai baƙinta na haske ne domin babu mai cemata baƙar fata, chaculate colour sannan ta haɗa da ido da kuma ƙaramin baki sai dogon hanci, itama tanada sumar gashi babu laifi bugu da ƙari kuma tanada ƙyakykyawar surar jiki, domin a dire take Lailah tafi Ayush da Maimoon dirin jiki, Lailah ganin kallon da Doctor Mansur yake mata babu ƙarshensa yasa ta matso daf dashi takai bakinta saitin fuskarsa tana hura masa iskar bakinta, a ruɗe yayi firgit ya dawo hayyacinsa yana sauƙe numfashi da smile a fuskarsa, ita kuwa komawa tayi ta zauna a yanda take tana binsa da kallo, wani irin yanayi yaji ya shiga lokaci guda daman hakane indai ya zauna a kusa da Lailah ya ɗan juma to saiya shiga cikin wani hali na feeling, ba shiri ya miƙe tsaye tareda faɗin "Baby zanje na ƙarasa Ayyukana amma zan dawo ba jumawa..." yana kaiwa nan ya nufi hanyar fita har ya buɗe ƙofa zai fita ta katse shi da cewa "JAAN..." juyowa yayi yana kallonta haɗe da sau mata ƙayataccen murmushi yace "My Baby..." turo ƙaramin bakinta tayi a shagwaɓe tace "yau ɗin ba chaculaty ne?..". Dariya yayi har saida fararen haƙwaransa suka fito yace "waya gaya miki ana fashin kawo wa Baby chaculate ne? na yau ma yafi na kullum..." sumbatar tafin hannunta tayi sannan ta hura masa iskar, yayi saurin dunƙule hannunsa kamar ya karɓi saƙon sannan ya ɗora hannun akan saitin zuciyarsa yana shafar wajen, Lailah cikin jin kunya takai hannayenta biyu ta rufe fuskarta tana dariya, shima da dariya yabar cikin ɗakin tareda rufe mata ƙofa.... Bayan fitarsa da awa ɗaya saiga Mommy ta turo ƙofar ɗakin Lailah da sallama a bakinta, lokacin Lailah har tayi nisa a baccin ta, zuwa tayi dab da gadonta ta zauna akan kujerar da yake fuskantar Lailah! zuba mata ido tayi tana tausaya mata a halin da take ciki, ga ta rasa tunaninta ga kuma Babban Yayanta a prison ga babu iyaye, tana cikin wannan tunanin taji ana faɗin "wacece ke? mezaki mu? kada ki cutar dani dan Allah, wayyo Doctor! Doctorr!! JAAN kazo ka temake niiii...." ta ƙarisa maganar tareda fashewa da kuka, ita kuwa Mommy kaɗa mata hannu take tareda cewa "A'ah Lailah ki saurare ni, nasan kin manta ni amma Ni ba cutar dake zanyi ba, ki kwantar da hankalinki..." Lailah girgiza mata kai take alamar bata gamsu da jawabanta ba, suna cikin wannan halin saiga Doctor ya shugo yana riƙe da baƙar leda, ya ƙarisa shugowa da sauri ganin yanda Lailah take ta kururuwa, zama yayi a bakin gadon ya kamo hannunta yana matsa mata a hankali, yace "colm down Baby, ki daina jin tsoron mutane domin sun zo duba lafiyarki ne bawai cutar dake ba, idan kikayi musu haka baki musu adalci ba, a yanzu kin mance komai but kina buƙatar ƙwanciyar hankali yanda zaki sake sabunta rayuwarki, waɗanda kika mance a baya yakamata ki dawo dasu cikin rayuwarki kinji koh Baby..." Lailah fashewa tayi da matsanancin kuka tana faɗin "kenam wannan mah inada alaƙa da ita? wacece ita a gurina ina buƙatar sani domin na karɓeta da hannu bibbiyu..." Doctor ya kalli mommy sannan yace "Hajia saidai kiyi mata bayani da kanki tinda har zata saurareki.." Mommy hawaye ne ya kuɓuto mata tasa hannu tana gogewa tareda matso da kujerar ta kusa da ita tace "Lailah ki ƙwantar da hankalinki wannan ƙaddarar daya afku dake Allah Ubangiji yasa shine mafi Alkhairi agareki, Allah yasa canjin rayuwarki shine silar shiryuwarki akan komai duk da bana shedar ki akan aikata laifi amma na sanki da yawan faɗa da masifa...". Mommy ta ƙarasa maganar cikin zolaya tareda ja mata hanci, itama Lailah saida ta murmusa jin yanda mommy taso da nishaɗartar da ita, Mommy ta cigaba da cewa "Ni Abokiyar mahaifiyarki ce wacce ta rigamu gidan gaskiya, ni nake yawan kula da al'amuranku ke da ƴan uwanki tin kuna yara da iyayenku suka rasu, kuna ƙirana da suna Mommy kasancewar kunbi bakin ɗana wato Junaid domin shi kawai na haifa..." Lailah ƙura mata ido tayi har saida ta kammala sannan tace "na fahimce ki Mommy, kenam iyayena tin ina ƙarama suka mutu suka barni? niɗin marainiya ce daman? Allah Sarki mommy mun gode miki da ƙoƙarin da kikayi akan mu, toh Amma su nawa ne ƴan uwana?.." Mommy tace "ku huɗu ne Lailah, Babban Yayanki shine Doctor Hasheem wanda yanzu haka yana prison, sai kuma wanda ya biyo shi shikuma yana ƙasar Egypt karatu, sai kuma haidar wanda yanzu yana can Katsina gurin kakarku, kece kawai mace acikinsu kuma Auta..." Lailah cikin yanayin tausayi tace "toh amma meyasa su ƴan uwan nawan basu zo sun dubani ba?.." Mommy tace "saboda gudun tashin hankalinsu hakan yasa ba'a sanar musu rashin lafiyarki ba kuma hatta shi babban Yayan nakun basu san yana prison ba, amma da yardar Allah Yayanki ya kusan fitowa..." Lailah tace "gwara ma da ba'a gaya musu ba saboda kar hankalinsu ya tashi, amma keɗin mommy ya sunan ɗan nakin?.." Mommy tayi ajiyar zuciya tana mai jinjina wannan al'amarin daya faru da Lailah, gashi wanda take mutuwar so mah ta manta dashi, cikin kasalalliyar murya tace "sunansa Junaid Khan yana da matarsa har ta kusan haihuwa..." Lailah tayi saurin katse mommy da cewa "a'a mommy daman ba cewa zanyi inasonsa ba, ni yanzu burina shine komai nawa ya dawo mun ƙwaƙwalwata..." Murmushi mommy tayi tana girgiza kai tace "Lailah kenam ni ɗin ma kawai nasar miki nayi saboda ki fara sanin kowa.." itama Lailah murmushi tayi tace "Allah Sarki mommy nima wasa nake miki kiyi haƙuri..." kaiwa hannu mommy tayi tana shafar suman gashinta ba tareda tace komai ba.. suna cikin wannan halin sai suka ji sallama an turo ƙofar ɗakin, Mommy da Doctor suka amsa sallamar cikin kulawa, Maimoon ce ta shugo da yaro a hannunta ta rufa masa farin towel a kansa, sai kuma Ammy da Daddy! Doctor ne ya nuna musu waran zama tareda musu barka da zuwa suka gaigaisa, itama mommy tana murmushi suka gaisa cikin aminci da kyautatawa juna, Daddy ne yazo har bakin gadon Lailah ya zauna yana faɗin "Autar Mama da Abba yadai?..." Lailah zuba masa ido tayi tana murmushi tace "babu komai..." Mommy tace "waɗannan ɗin kin ganesu ne?.." Lailah tana kallonsu tace "na ganesu mana ai suna yawan zuwa mun, kuma Doctor ya ce mun suna taka rawar ganin na samu lafiyata..." Daddy yace "ni naso ace ma asibitin ƙasar waje aka fita da ita wata ƙila za'ayi dacen dawo mata da memory sense ɗinta..." Lailah tayi saurin katse shi da cewa "a'a Daddy nafi jin daɗin zamana a wannan asibitin domin Doctor yana bani kulawa sosai da sosai.." ta ƙarasa maganar tana kallon Doctor Mansur wanda shima kallonta yake yana murmushi ... Daddy yace "toh shikenam ai naga yanzu kin samu lafiya koh?.." jinjina kai Lailah tayi tareda cewa "sosai ma Daddy yanzu bana jin komai a jikina" Daddy yace "Masha Allah haka nake son ji Autar Abba, Daman yau nazo ne ma akan a sallameta zamu wuce gida da ita, akwai ƴan uwan mahaifiyarta cikin wannan satin zasu zo duba jikinta, ƙwanaki ƴan uwan mahaifinta ne suka zo, insha Allahu zan cigaba da riƙeta a gidana..." Mommy tana zaune a gefe guda tace "Allah Sarki gaskiya rankayadaɗe kana kokari kam ka riƙe zumunci sosai, kace daman kuna ziyartar ta shiyasa ta saba daku..." Murmushi kawai Daddy yayi domin kafin mahaifinsu ya rasu ya rigada ya bashi amanar yaran, kuma yaso su Doctor Hasheem su dawo gidansa da zama amma fur yaƙi yadda yafi son zama agidan iyayensa ganin haka yasa su Lailah suma suka ƙi tafiya subar gidan, kuma sunƙi zuwa gurin ƴan uwan iyayensa domin su ɗin haɗamammu ne suna harin dukiyar da aka bar musu ne... Lailah tana zaune taji Ammy tana faɗin "nidai na ƙosa naji Lailah tamun magana amma taƙi kulani.." Dariya Lailah tayi tace "wallahi Ammy mantawa nayi, amma amun Afuwa .." Ammy tace "toh na miki Afuwan, gashi yau nazo miki da ƴar uwarki Maimoon da jaririnku..." Lailah tana dariya tareda leƙen fuskar Maimoon tace "laaa daman itace Aunty Maimoon ɗin da kikace ita kaɗai ce ɗiyarki kuma ta haihu? Ayyah gashi kuwa kyakkyawa tanada kyau, shin zan iya ganin jaririn namun?..." Maimoon murmushi tayi sannan tace "ba komai gashi nan.." ta tashi ta miƙa mata yaron tana mamakin yanda rayuwa ta sauyawa Lailah, gashi har itama ta mantata... tana cikin wannan tunanin Lailah ta katseta da cewa "ya sunansa?" Maimoon tace "Abubakar amma inkiya kuma Rapeekh.." "Kaii kai kaii suna mai daɗi gashi shima Balarabe ne fari tas, ya ɗauko farinki amma ban saniba ko Babanshi ma fari ne ko kuwa baƙi, amma ina Abban shi yake?.." a cewar Lailah wacce idonta ke kan yaron, Maimoon sunkuyar da kanta tayi ƙasi domin batada bakin magana, sai Ammy ce tace "Abbansa baya gari yayi tafiya ne.." tace "Ayyoh..." Bayan wasu seconni Lailah ta fara shessheƙar kuka ga yanda hawaye ke zubo mata, hannunta kuwa yana riƙe da yaron, gaba ɗayansu kallonta suke cike da mamaki, "daga wasa da dariya sai kuma kuka?".. a cewar Daddy yana kallonta, kanta a sunkuye take cewa "ina son ganin halin da Yayana yake a prison, inason ganinsa ko hankalina zai ƙwanta, bansan ya kamannunsa yake ba, Yayana bai kamata ace yana zaune a prison ba yanda muke da dukiya kamar kamar...." lokaci guda ta sake fashewa da kuka na gaske, Doctor gaba ɗaya hankalinsa a tashe yake domin ba'a son tana yawaita kuka saboda ana buƙatar hutawar ƙwaƙwalwarta, dasauri ya miƙe tsaye yana faɗin "kinga Baby ki ƙwantar da hankalinki yanzu za'a kaiki bana son yawan kukan ki, shin kinaso na shiga damuwa?..." dasauri ta girgiza masa kai alamar a'ah yace "toh banason kukan ki, idan kuma kinason na shiga damuwa shikenam cigaba da kukan..." share hawayenta tayi tareda cewa "na daina JAAN bazan ƙara ba, amma ku kaini gurin Yayana dan Allah..." Daddy yace "to zamu kai ki yanzu kuwa, daga nan sai mu wuce gida ko?.." Lailah kamar zatayi kuka jin za'a wuce da ita gida tace "kenam na daina ganin JAAN?.." Doctor yace "a'a zaki rinƙa ganina akai akai kinji, babu yanda za'ayi nayi nisa dake Baby..." murmushi tayi sannan tace "Nagode JAAN..." mayar mata yayi da martanin murmushi duk da shima ransa ya sosu sosai jin Lailah zata koma gida, yanzu ba kullum zai rinƙa ganinta ba... duk waɗanda suke wajen babu wanda bai fahimci alaƙar dake tsakanin Doctor Mansur da Lailah ba saidai su nasu soyayyar a bayyane take amma sirrinta tana cikin jijiyoyinsu wanda har yanzu basu fito fili sun sanar cewa suna son junansu ba, Bayan an shirya Lailah fita akayi da ita waje saboda motar tana harabar hospital, tana fita waje taji kamar ba'a duniya take ba, ga rana wanda ta daɗe bata saka shi a ido ba, wani irin haske garin yayi mata saida ta nemi a bata glass dasauri Doctor ya ciro glass ɗin idonsa ya sanya mata, daga nan ta fara ganin daidai, cikin yanayin damuwa Doctor ya kamo hannun Lailah tareda miƙa mata ledar hannunsa yace "Baby ga chaculaty nakin..." tana sharar hawaye ta karɓa tana godiya... shiga motar sukayi Lailah da Maimoon a bayan seat sai kuma Ammy da Daddy a gaban motar, Daddy ne mai driving ɗinsu, A yayin da ita kuma Mommy ta shiga motarta tabi bayansu kai tsaye Prison suka nufa... Doctor Mansur ya juma a tsaye a harabar hospital yana jimamin tafiyar Lailah.... ★★★★★★ Hafzat tana zaune a falo tin ɗazu ko motsawa batayi ba, tana kallon tv taji anata knocking ƙofar falo, a tunaninta mommy ce ta dawo dasauri ta tashi taje ta buɗe, ganin wanda yake knocking ne yasa ta tsaya tana masa kallon rashin sani, wani farin mutumi ne gabjejen soja yake tsaye shima binta yake da kallo daga sama har ƙasa, shigarta ba ƙaramin burgeshi yayi ba tana sanye da blue jeans dogo da kuma riga t-shirt mai dogon hannu, gata gajeriya ƴar ɓulɓul da ita, hips ɗin nan ya zauna ga breast a ɗage, ƴar kyakkyawar bafulatana! ganin yanda yaketa kallonta ne yasa ta motsawa tace "ina wuni..." ƙayataccen murmushi yasau mata tareda faɗin "your welcome Baby girl..." sunkuyar da kanta ƙasi tayi tana wasa da yatsunta, ta kuma ji yace "Oga yana ciki ne?.." ɗagowa tayi tana kallonsa cikin rashin fahimta ba tareda tace masa komai ba girgiza kai yayi sannan yace "hala bakya jin Hausa koh?..." murya ciki² tace "waye Oga?.." murmushi ya kuma yi dake sojan yana da sauƙin kai yace "maigidan nan toh.." Dasauri ta ɗaga masa kai tareda faɗin"eee yana nan" yace "ok bani guri na wuce mana kodai kina mun rowar shiga falonku ne..." matsa masa tayi tana girgiza kai, yace "jeki ƙira mun shi toh" jiki a sanyaye ta wuce kai tsaye upstairs ta haura, shi kuma zama yayi akan sofa yana bin bayanta da kallo, yana ƙwance akan gado sai faman sharar bacci yake, a cikin baccin ne yake jin knocking a hankali yake buɗe eyes ɗinsa daƙer ya iya motsa lips ɗinsa yace "waye?.." cikin kakkarwar murya tace "Uncle ni ce.." "Ok come in" turo ƙofar tayi a hankali ta shugo kanta a ƙasi saboda gudun yanda zata ganshi, ganinta yasa ya tashi tareda sauƙe ƙafarsa ƙasan carpet daga shi sai 3quater zuwa cinyarsa ko riga babu a jikinsa, tasowa yayi yana takawa a hankali kamar mai tambayar ƙasi yazo har gabanta yana yamutsa fuska irin baccin nan bai gama isar sa ba yace "keee..." a ɗan ruɗe ta ɗago ta kalle shi, gabanta ne yayi wani irin bugawa da ƙarfin gaske ganin jikinsa fari sol duk gargasa ga ƙirar ƙarfi tinin ta ruɗe murya na kakkarwa take faɗin "Daman! Daman! Damann wani ne ya zo nemanka...." hannu yasa ya ɗago da haɓarta yana kallon fuskarta yace "meyasa kike jin tsoro na? nayi miki kama da dodo?..." dasauri take girgiza kanta kamar ta rausa ihu haka take ji tsabar tsoro da fargaba, kuma tana tsoron kar Aunty Ayushert tazo ta tarar da ita a cikin ɗakinta ga kuma mijinta a ɗakin. tana cikin wannan tunanin taji yace "waye yazo nema na?..." da sauri tace "wallahi ban sani baa amma soja ne..." Allah! Allah take tabar ɗakin nan domin kwarjini ɗakin yake mata domin bata taɓa shugowa cikin ɗakin nan ba sai yau... ƙura mata ido yayi yaɗan sau mata murmushi ba tareda ta sani ba sakamakon kanta dake kallon ƙasan carpet yace "ki daina jin tsoro na kinji ko? ki ɗauke ni a mazannin uncle ɗinki..." Kaɗa masa kayi kawai tayi ba tareda ta ce komai ba, ya kuma cewa "kije ina zuwa..." sai a lokacin taji wani sanyi a ranta kamar zata dungura ƙasi haka ta tafi a gaggauce ko waiwayowa bata yi ba, jiki a sanyaye ta sauƙo falo tace "yana zuwa.." ta ƙarasa maganar tareda wuce zata koma ɗakinta taji mutumin ya dakatar da ita "please wait..." juyowa tayi tana kallonsa fuska kamar zatayi kuka tace "Na'amm.." fuska a sake yace "zo ki zauna mana" ta girgiza masa kai tareda cewa "inaso zan shiga ciki ne" "ban yarda ba to, kizo ki zauna anan" ya ƙarasa maganar yana nuna mata wurin da zata zauna a kusa dashi, zaro ido tayi tace "kayi haƙuri zan zauna anam" ta ƙarasa maganar tareda ɗosana ɗuwawunta akan sofa mai ɗaya wanda yake ɗan nesa dashi, Murmushi yayi tareda cewa "wooo this girl..." ita kuwa kai a sunkuye fuska ba Annuri domin ba ƙaramin takurata yayi ba, bata ankara ba taji shi a kusa da ita ya zauna akan hannun kujerar da take, yasa hannu ya tallafo kanta suna kallon juna yace "fatan dai ban takuraki ba ko?.." dasauri ta girgiza masa kai tareda kawar da kanta gefe, a hankali ya furta "meye sunanki?.." a saitin kunnenta, ɗagowa tayi ta kalle shi sannan tace "Hafzat..." yace "wow Nice name, Ni kuma *Judan*..." ya kuma cewa "ajinki nawa a school?.." tace "aji 3.." yace "wow congrats kina level 3 but which university?..." ɗan turo lips ɗinta tayi sannan tace "a Sacondary fa nake.." juyar da eyes ɗinsa yayi yana faɗin "sacondary duk girmanki? how old are you?.." kamar baza tayi magana daga ƙarshe tace "18 years old..." hannu yasa rufe bakinsa yana ƙunshe dariyar ciki yace "wooo kice girman bread kika yi.." Hafzat takaici kamar zai mata mai cikin ranta take cewa "wannan akwai ɗan rainin wayo wallahi, amma shikenam yanzu komai ya tambayeni bazan kulashi ba wallahi, gaba ɗaya ya takurani..." tana cikin wannan zancen zuci taga Uncle Junaid ɗinta yana sauƙowa daga saman stairs iya farar jallabiyarsa kawai ya ɗora, shi kuwa Judan bai ma san Oga Junaid ya sauƙo ba, idonsa akan Hafzat ko ƙibtawa baya yi, yarinyar tana matuƙar burge shi, Ogah Junaid tsayawa yayi tareda goya hannayensa ta ƙirjinsa idonsa akan Judan, Hafzat cikin tsoro tace "ga nan Uncle.." waiwayawa yayi suka yi ido huɗu Judan yace "your welcome Ogah.." ya ƙarasa maganar yana sosa ƙeyarsa tareda miƙewa tsaye daga zaman da yake a hannun kujerar da Hafzat take, ya koma cikin kujerar gefe da ita, shima Junaid zuwa yayi ya zauna yana faɗin "sannunka Judan, wato kazo ka samu yarinya shine zaka shishshige mata koh?..." Hafzat dasauri ta tashi tabar falon ta koma cikin ɗakinta wanda yake gefe dana Mommy.... 𝑡𝑦𝑝𝑖𝑛𝑔✍️ 𝗠𝗔𝗧𝗔𝗥 𝗗𝗔𝗠𝗨𝗦𝗔 the wife of a tiger🐅🐅🐅🐅 𝙼𝚊𝚕𝚕𝚊𝚔𝚒𝚗 𝙰𝚜𝚖𝚎𝚎𝚝𝚊𝚑 ✍️✍️ 𝙿𝚊𝚒𝚍 𝚋𝚘𝚘𝚔 𝚌𝚊𝚕𝚕 𝚘𝚛 𝚠𝚑𝚊𝚝𝚜𝙰𝚙𝚙 09065443871 *💫💫{{N W A}}💫💫* Book two C̶h̶a̶p̶t̶e̶r̶ 66 to 70 Bayan isar su prison suka tarar da Doctor Hasheem acikin wani irin hali gaba ɗaya ya fita hayyacinsa, duk ya rarrame yayi baƙi ƙirin, a zaune suka tarar dashi guri guda wajen da babu jama'a sai iya shi kaɗai, Allah ne kaɗai yasan abunda ke damunsa ya kifa kansa da gwiwa, ɗayane daga cikin security prisoner ya rakosu har waranda yake Mommy tana ganin yanda Hasheem ya koma da gudu ta ƙarasa wajensa tana ƙiransa "Hasheem!!! Innalillahi wa inna ilaihi raju'un haka ka koma? dubeka kamar mahaukaci subhanallahi..." Daƙer Hasheem ya ɗago yana kallonsu ɗaya bayan ɗaya duk yunwa ya gama cinye shi domin baya samun damar cin abinci saboda tsananin damuwar da yake fama dashi, Maimoon gaba ɗaya jikinta ne ya ɗau kakkarwa ganin halin da Hasheem yake ciki har hawaye sun soma zubo mata, tayi saurin sunkuyar da kanta ƙasi sabida kar Daddy ya ganta ga jariri kuwa a hannunta... cikin firgici da ruɗani Lailah tace "wannan ne Yayan nawan? ya naganshi kamar Almajiri marar gata anya kuwa shine Yayana? kaiii ina tantama nidai dan Allah a temaka a kaini gurin Yayanaaa..." lokaci guda ta fashe da matsanancin kuka, Ammy ce ta dafa kafaɗarta tana bubbuganta alamar rarrashin tace "Lailah kiyi haƙuri wannan shine Yayanki" Lailah shuru tayi ta sake baki tana kallon Ammy cike da mamaki lips ɗinta har rawa yake kamar maijin sanyi tace "wai da gaske ne wannan shine Yayana?.." Ɗaga mata kai Ammy tayi... shi kuwa Daddy juyawa ya yi yayi tafiyarsa, zuwa yayi ya buɗe murfin motar ya zauna domin bazai juri ganin Hasheem a cikin wannan halin ba kuma bazai fitar dashi daga prison yanzu ba.. Lailah zuwa tayi gaban Hasheem jiki na ɓari gudun kar taje mahaukaci ne domin yanayinsa ba maraba da mahaukacin, Ga ya tara wani mahaukacin suma akansa zuwa gemunsa ga yayi baƙi ƙirin ga kuma kayan jikinsa yayi duƙwi-duƙwi tsabar datti don ko wanka baya samun halin yi bare wanki, durƙusawa tayi a gabansa tana sharar hawaye tace "Yaya..." shima kallonta yake cikin tausayawa ya kamo hannunta duk biyun yana zubda ƙwallah yace "Ƙanwata Lailah naji daɗi ganinki, kin samu lafiya sosai Alhamdulillah.." itama tana kuka tareda faɗin "Yaya haka ka koma? a photo kafi haka kyau sosai, meyasa aka kawo ka nan Yaya?..." Girgiza kai Hasheem yayi sannan yace "kiyi haƙuri Auta zan cigaba da zama anan, kedai ki rinƙa mun Addu'a kinji ko?..." kuka ne ya kuɓuto mata da gudu ta tashi tayi waje tana kuka.. shima sunkuyar da kansa yayi ƙasi yana kuka mai cin rai, mommy ce ta dafa shi tareda cewa "kayi haƙuri Hasheem komai yayi farko zaiyi ƙarshe, mahaƙurci mawadaci insha Allahu zaka fito daga cikin kurkukun nan, zamanka anan bai dace ba..." Ɗagowa yayi yana kallon mommy da jajayen idanuwansa wanda yasha kuka yace "a'ah mommy ku barni kawai na ƙarasa rayuwata anan, nan shine daidai dani, na tafka babban kuskure arayuwata, abunda ban taɓa aikatawa ba yau gashi an wayi gari nayi abun kuma hakan yayi sanadiyar shugowata gidan Ajali nah, ina fatan daga nan sai ɗakina na gaskiya wato kabarina, nan shine daidai da rayuwata, idan na fita daga nan da wani ido zan dubi waɗanda suke ganina da mutunci? shin mezance musu? na rigada na zubar da kimata da kuma mutuncin ahalin mu, wallahi tallahi Ni ba mutumin banza bane, ƙaddara ce tasa na aikata hakan, kunya bazai barni na fita daga cikin prison ɗin nan ba, dan Allah ku barni na mutu a cikinsa....." yana kaiwa nan ya sake fashewa da wani irin matsanancin kuka.. Itama mommy kukan take domin ba ƙaramin tausayi ya bata ba, girgiza kai Ammy tayi tace "Allah Sarki abun tausayi, wallahi ko kaɗan banso anzo wannan gacin ba, naso ace an warware matsalar nan a cikin gida ba tareda kowa ya sani ba, amma Alhaji ya kama ya shigar da ƙara, gashi nan ai yanzu magana ta bazu ko ina, yanzu Maimoon bata shiga cikin mutane itama ko gurin ƴan uwanta bata zuwa saboda ƙyararta da sukeyi wai tayi cikin shege abunnan yana damuna matuƙa wallahi...." itama Ammy fashewa tayi da kuka ta juya ta nufi hanyar fita tana kuka... Mommy miƙewa tayi tsaye tareda riƙo hannunsa tace "tashi tsaye maza kayi haƙuri" shima miƙewa yayi da temakon mommy domin a halin yanzu bashida wani sauran ƙarfi a jikinshi, ta jawo shi sukazo har gaban Maimoon wacce take tsaye itama da yaronta sai faman kuka take kanta a gefe guda, Mommy ta karɓi Rapeekh a hannunta sannan ta miƙawa Hasheem tace "nasan tinda aka haifi yaron nan baka ganshi ba, toh yanzu ka karɓeshi ka sanya masa albarka tinda mahaifinsa yana raye, ga jininka kaima insha Allahu duniya bazatai muku dariya ba..." Hasheem karɓan yaron yayi ya ƙura masa ido yana zubda hawaye daga baya kuma ya fara jero masa addu'o'i yana tottofa masa, daƙer ya buɗe bakinsa yace "meye sunansa?..." yayi maganar idonsa akan Maimoon wacce itama kallonsa take, a yayin da ita kuma Mommy tabar wajen ta basu guri, kamar baza tayi magana ba a hankali tace "Rapeekh" jinjina kai yayi sannan yace "shine asalin sunansa?..." tace "sunan mahaifinka ya samu.." a hankali Hasheem ya ambaci sunan yace "Abubakar..." Idonsa akan yaron baisan lokacin daya sau murmushi ba lokaci guda yaron ya shiga zuciyarsa, ji yake kamar bazai bayar da yaron ba, shima yaron dake akwai wayo sai kallon uban yake yana buɗe ƙaramin bakinsa alamar dariya, Kallonta yayi yana murmushi yace "yayi wayo sosai yanzu watansa nawa?..." tace "a ranar daka shugo prison a ranar aka haifeshi..." dasauri ya maida idonsa kan yaron yana mai tausaya masa yace "kenam yanzu watansa biyar?..." ɗaga masa kai kawai tayi ba tareda tace masa komai ba, doguwar ajiyar zuciya yaja ya juyo yana fuskantar Maimoon a hankali ya ambaci sunanta "Maimoon.." ɗagowa tayi itama tana kallonsa saida suka ɗau tsawon minti guda suna kallon junansu cikin tausayawa juna daga bisani yace. "dan Allah na roƙe ki da sunayen Allah ki yafe mun abunda nayi miki, nasan banyi miki daidai ba kuma nasan kin tsane ni amma ki gafarce ni, ina tsammani mutuwa yau ko gobe banason na mutu da hakkinki akaina, yau idan kika ce kin yafe mun kin gama mun komai! daman kullum tunani shine aina zan ganki in nemi yafiyarki...." kafin ya rufe baki ta katse shi da cewa "Bani yarona..." buɗe baki yayi zai mata magana tayi saurin dakatar dashi ta hanyar tsawa tana faɗin "nace ka bani yarona ko kai ka haifa mun shi ne?..." kamar zaiyi kuka yace "gashi nan toh amma kice kin yafe mun dan Allah ko zan ji daɗi a raina..." hannu tasa ta karɓi yaron cikin fushi, a farko taji tausayinsa amma yanzu ya fama mata tabon dake cikin zuciyarta, idan ta tuno da abunda yayi mata ji take kamar ta fasa masa kai da bullet, ita murna ma taji da Babanta ya tura shi prisoner... juyawa tayi zata tafi ba tareda tace masa komai ba yayi saurin riƙo hannunta yana faɗin "dan Allah Maimoon ki temaka mun, idan kika tafi bansan ranar dazan ƙara ganinki ba, kuma ina buƙatar yafiyarki domin inaji a jikina mutuwa zanyi..." A fusace ta juyo tana faɗin "toh sai mai idan ka mutu? shin mutuwarka zai dameni ne? ko yaronka mutuwarka bazai dameshi ba balle Ni, ka sake mun hannu na nikam idan kuma kana son maimaita mun fyaɗen toh Bismillah..." Jikinsa na kakkarwa yace "Mai Mai Maimoonnn..." "Shurt up bana buƙatar jin komai daga gareka wallahi tallahi I hate you" a tsawace tayi masa maganar dan dai babu kowa a wajen da babu abunda zai hana mutane taruwa a gurin, ta cigaba da cewa "ka lalata mun rayuwata, ka watsar mun da mutunci na, nasan babu sona a cikin zuciyarka hasali ma tsanar da kake mun ne yasa ka aikata mun fyaɗe, kuma yarinyar da kake so ina maka albishir da cewa itama ka rasata domin yanzu haka tana gidan mijinta wato Junaid da tsohon cikinta, kamar yanda ka rasata haka nima ka rasani har Abada Abadan Abaadann! kuma ka rasa yaronka ma daga yau ne bazaka ƙara ganinsa ba saboda gobe ma insha Allahu zan bar ƙasar nan, bazan dawo ba kuma, idan kaga dama ka mutu acikin prison bai dameni ba, Mtsswww...." tana kaiwa nan a fusace juyawar da zatayi taga Lailah tana tsaye ta bayanta sai faman zubda hawaye take ta kuma goya hannayenta biyu ta gaban ƙirjinta, Maimoon tsayawa tayi tana kallonta domin bata san tin yaushe take tsaye a wajen ba, ganin babu abunda zata ce mata ne yasa ta ratsa ta gefenta tayi tafiyarta, Lailah tana kuka ta ƙaraso gaban Hasheem tace "Yaya fyaɗe kayi mata? hakan yasa aka kawo ka prison? kenam yaron hannunta kaine Babansa? innalillahi wa inna ilaihi raju'un..." Doctor Hasheem shima kukan yake yace "Lailah na aikata kuskure, ina neman yafiyar Maimoon..." tace "Yaya ba abunda zan iya a wannan al'amarin, bazan iya tuna komai ba Yaya, ban san mai zance ba, duk tattaunawar da kuka yi akai duk naji su, amma bayan yanzu dana saurara bansan komai akai ba na manta wallahi, kayi haƙuri Yaya...." tana kaiwa nan itama ta juya da gudu ta tafi tana kuka, Durƙusawa yayi da gwiwowinsa ya ɗora hannayensa biyu a kayi yana faɗin "Innalillahi wa inna ilaihi, Subhanaka inni kuntu mina zalimin, Allahumma ajurni fii musibati wa akhlif li khairan Minha....." daga nan numfashinsa ya ɗage cakk ya faɗi ƙasi sumamme, tsabar damuwa da ƙuncin da yake ciki.... Ita kuwa Mommy tin fitar ta na farko bata tsaya sauraron kowa ba haka ta shige motarta taja tayi tafiyarta, Itama Lailah turota akayi akan tazo ta ƙira Maimoon su tafi tazo ta tarar dasu suna wannan maganar har taji, suma bayan fitarsu jan motar Daddy yayi da gudu yabar prison kai tsaye gida suka nufa, kowa a cikinsu ba wanda ya kula kowa, ita Maimoon ta rufe fuskarta da mayafin jikinta in banda kuka ba abunda take yi, itama Lailah kukan take ciki², Sai Ammy da Daddy dake gaban motar....... Bayan tafiyarsu Maimoon Doctor Hasheem yana ƙwance a ƙasi yakai kusan awa guda ba motsi ba kuma wanda ya ɓullo ta waran balle ayi masa temakon gaggawa, saida wani daga cikin prisoner yazo duba shi yaganshi shame-shame a kwance da gudu ya tafi ƙiran masu kula da su... ★★★★★★ Ata ɓangaren su Junaid kuma yana zaune da baƙonsa wato Soja Judan, An aiko shi ne domin ya kawo saƙo daga ƙasar california shima ba sojan Nigeria bane daga can yake bayan rasuwar Angel ne aka bashi miƙamin Angel wato Commander California Army, kafin ya isar da saƙonsa saida ya tambayi Junaid cewa "Ogah wannan yarinyar anan gidan take?..." Junaid kallonsa kawai yake cike da mamaki yana zancen zuci cewar "abun zai ban mamaki gaskiya, shin yaushe Judan ya fara son mata? ni a sanina dashi bai cika kula mata ba ko kallonsu bayayi toh ya akayi daga haɗuwa da Hafzat har ya fara zaucewa haka...." yana cikin tunani Judan ya katse shi da cewa "Ogah yadai kodai ka shiga tunani ne daban, wallahi Oga this girl she is a beautiful I like her.." zaro ido Junaid yayi yana kallonsa ko ƙibtawa bayayi sai yanzu yayi ƙarfin halin cewa "Judan yaushe ka fara soyayya?..." Murmushi yayi sannan yace "akan wannan yarinya na fara jin shauƙin soyayya, ina ido huɗu da ita naji wani irin sauyin duniya..." kawar da kai Junaid yayi yana ƙunsar dariya domin ba ƙaramin dariya Judan ya bashi ba, ya kuma cewa "but Oga ina zaku bani ita?..." girgiza kai Junaid yayi sannan yace "makaranta takeyi yanzu! kuma ai bani ne mai bayar da ita ba.." Judan yace "Ni ko ainane zanje a bani ita idan ta kammala karatunta..." murmushi kawai Junaid yayi ba tareda ya kuma cewa komai ba, Judan yakai kusan minti biyu bai ce komai ba idonsa a gefe guda sai faman zuba murmushi yake shi kaɗai, Junaid ganin zama shurun ya ishe shi haka yasa yayi masa gyaran murya tareda faɗin "toh baban love yanzu dai a sanar mun saƙona kafin ka shiga tunanin ka..." Dasauri Judan yasa hannu a aljihunsa ya ciro wata takarda ya miƙa masa tareda cewa "gashi saƙone daga ƙasar california Chief of Army's yana son ganinka next month..." Junaid cike da mamaki yace "meyasa Chief of Army's California yake son ganina alhalin ga manya-manyan sojoji ba'a nemesu ba sai Ni da nake Captain kuma zuwa yanzu kam na ajiye aikin..." Murmushi Judan yayi sannan yace. "kai kafi cancanta a nema basu ba, sannan bakada labarin kowa an ƙaƙƙara masa matsayi acan california? nima yanzu haka miƙamin Angel aka bani, yanzu dai ka buɗe takardar ka karanta saƙonda yake ƙunshe a ciki..." Jinjina kai Junaid yayi tareda yin Bismillah ya fara warware takardar yace "Allah yasa muga Alkhairi" Idonsa ya kafa akan rubutun ko ƙibtasu bayayi lokaci guda kuma ya miƙe tsaye a zabure yana zazzaro dara-daran idanuwansa dasauri yakai idonsa kan Judan yana masa kallon rashin fahimta, Murya na shaƙewa yace "wai dagaske ne Judan kodai tsokana kazo yi?..." Murmushi Judan yayi yace "haba Ogah yanzu saboda tsokana saina taso tin daga California nazo Nigeria? ka duba signing ɗin manya-manyan mutane ne da kuma manyan sojoji a jikin takardar, yanzu ka zama babban soja mai faɗa aji..." "toh amma meyasa sai ani za'a bawa wannan matsayin hakan ma a ƙasar da ba namu ba?..." a cewar Junaid wanda gaba ɗaya ya ruɗe ganin wannan letter. tashi yayi shima Judan yazo har gabansa ya tsaya suna fuskantar juna yace "Ogah a duk faɗin ƙasar california da China da Pakistan da Italian da indian da Nigeria da duk sauran sojojin ƙasashe babu mutum ɗaya wanda aka samu ya iya yaƙar Babban matsafi kamar Munafurr ba sai kai, babu wanda ya iya yaƙar namun daji na tsafin Munafurr sai kai da kuma marigayiya Angel, sojoji waran trillions duk mun rasasu a sanadin yaƙin nan iya kai kaɗai ne kawai ka tsira da rayuwarka, kai ka cika babban jarumi! a duk ƙasar california da sauran ƙasashe duk suna alfahari dakai da kuma jarumtarka, yanzu haka kana shiga headquarters na ƙasar california zaka ga mutum mutuminka a mashigar facility, saboda haka ne yasa aka yanke shawarin zaka zamo General na sojojin california, wannan shine takardar shaidar...." Junaid kawai binsa yake da kallo gaba ɗaya ya kasa cewa komai tsabar farin ciki sai cewa yayi "yanzu saboda wannan yaƙin da akayi ne yasa aka bani matsayin General? hakan ma na ƙasar california?..." "ka cancanci haka ne shiyasa..." jin muryar mutum ata bayansu ne yasa suka waiwaya da sauri suna son ganin ko waye wannan, ganin sarki Raamud ne yasa Junaid ya nufi waransa da fara'a yana faɗin "Abbah saƙon ƙarin matsayi aka kawo mun..." sarki Raamud yana murmushi yace "Junaid kenam ai nafika sani tinda nima saida aka kawo mun takardar nasa hannu..." Junaid baki ya gagara rufuwa yace "kenam kaima harda signing ɗinka acikin takardar?..." Jinjina kai kawai sarki Raamud yayi tareda ƙarasowa cikin falon ya nemi kujera ya zauna, suma Junaid da Judan zama sukayi kowa da Annuri a fuskarsa, sarki ya kalli Judan da fara'a a fuskarsa yace "sannu da isowa Judan kaine ɗan aika kenam, kazo kuma matan gidan basa nan gashi ko lemo ba'a kawo maka ba..." sai a lokacin Junaid ya tuna ashe dai ba'a kawowa baƙo ruwan sha ba, da hanzarinsa ya miƙe tsaye ya nufi kitchen cikin sa'a kuwa ya samu abinci a flask da miyan ferfesun chicken ya ɗora plate da spoon akai ya kawo masa kan dinnig table sannan yaje ya buɗe frig ya ɗauko lemon juice da farro na ruwa sannan ya haɗo masa da kayan fruits yazo ya jejjera kayan abincin, ya ɗauki wuƙa yayi slice ɗin kayan fruits akan glass tray, saida ya kammala haɗa komai tukun ya ɗago masa hannu yayi masa alama da yazo yayi lunch, tasowa yayi da murmushi akan fuskarsa ya nufi wajen dinnig yanda Junaid ya haɗa masa kayan food, har ya fara cin abincin ya dakatar tareda cewa "kashhh ..." Junaid har zai bar wajen yaji sautin Judan da sauri ya juya tareda tambayarsa "lafiya kuwa?..." Ɗan turo bakinsa yayi yace "banga wannan ruwan tea ɗin da mommy take haɗawa ba, cikin rashin fahimta Junaid yace "wani tea kenam, oh tea kakeso a haɗa maka?.." Judan yace "No no nooo akwai wani tea wanda mommy take haɗawa ba tareda tasa milk da sauran haɗe haɗe ba, kuma akwai daɗi sosai domin ban taɓa shansa ba sai randa nazo gidan nan..." Ɗan tsuka Junaid yayi sannan yace "kace empty tea kake so mana"... Judan rufe idonsa yayi tareda faɗin "Kashhh ka kasa fahimta ta..." Sarki Raamud yana daga kan sofa yana jin draman da suke yi sai faman ƙunshi dariya yake, shi Junaid ne yafi bashi dariya da har baƙo ma yasan kalar girke girken Hajia Fateema amma shi har yanzu ya kasa gane wani irin shayi Judan yake masa magana akai ba, ganin Junaid bazai gane ba yasa yayi gyaran murya tareda faɗin. "Junaid tsawon shekaru kana tareda mahaifiyarka amma baka san wani irin shayi takeyi mai daɗin gaske ba..." Junaid yace "toh kunata cewa tea marar milk toh ai Ni bazan iya sha ba tareda milk ba.." Sarki yace "yana nufin shayin na'a-na'a kasan akwai wasu saiwowi da take sawa masu daɗin gaske, sai sugar amma duk wanda yasha saiya manta ƙofar gidansu ....? "Okayyy na tuna, wannan haɗin kam sai mommy don ni bansan yanda takeyi ba, saidai ka jira ta dawo tinda ba yau zaka koma ba..." a cewar Junaid! Girgiza kai Judan yayi tareda faɗin "gaskiya I can't wait, a ƙira Hafzat tazo ta haɗa mun..." Sarki yace "ehh tinda tana nan ita saita zo ta haɗa maka, ai naga duk wacce ta zauna agurin Hajia saita koyi komai na girki da sauran abubuwan zamani..." Junaid yace "ok bari na ƙira maka ita.." ya wuce yana jinjina kai shidai yasan wayon Judan kawai so yake ya kalleta shiyasa ya fake da hakan... kai tsaye ɗakin Hafzat ya wuce, Hafzat tana ƙwance asaman katafaren gadonta tana lumshe da ido kamar mai yin bacci ƙwatsam taji bugun ƙofa a hankali, tana son tambayar ko waye amma hakan ya gagara daƙer ta tashi jiki a mace tana jan ƙafa taje ta buɗe ƙofar, ganin Junaid yasa ƙirjinta yayi wani rass dasauri taja da baya domin tinda tazo gidan nan bai taɓa zuwa koda bakin ƙofar ɗakinta ba sai yau, Junaid tsayawa yayi yana kallonta cike da mamakin irin tsoron da take masa, baisan dalilin da yasa take jin tsoronsa ba, nafarko shi ba wani haɗe mata rai yake yi ba, har yanzu bai nuna mata asalin kansa ba amma duk da hakan tana nuna tsoronta akansa, hakan kuma yana shirin sosa masa zuciya, ƙarasa shugowa yayi ya nemi guri ya zauna a bakin gadonta idonsa akanta yace "zo ki zauna" jiki na ɓari ta soma girgiza masa kai alamar a'ah, ƙara maimaita mata yayi kuma du ta sake girgiza masa kai, ransa ne yayi matuƙar ɓaci yakai hannunsa saitin goshinsa yana murzawa cikin zafin nama ya zaburo ya cabko hannunta sannan ya janyo ta dab dashi yana zaro mata ido yace "zauna nace..." ba shiri ta ɗosana ɗuwawunta a bakin gadon tana ajiyar zuciya, ba tareda ya kalleta ba yace "me kike tunani akaina ne?..." shuru tayi masa ba tareda ta bashi amsa ba, ya kuma cewa "nayi miki kama da dodo ne ko kuma kina tunanin zan cutar dake ne?...." kanta a sunkuye ta kasa ɗagowa balle ta iya bashi amsa, ransa ne yayi matuƙar ɓaci a fusace ya daka mata tsawa tareda faɗin "I hate dis nonsense, idan ina miki magana kina sharar dani wata rana zanyi ball dake ..." Hafzat a gigice ta ɗago tana kallonsa lips ɗinta na kakkarwa tama rasa mai zata ce masa, . haka kawai Junaid yake mata ƙwarjini tin daga lokacin data fara ganinsa ta soma jin shakkarsa domin ta juma bataga namiji dirarre ƙarfaffa mai faffaɗar ƙirji irin na Junaid ba, gashi asalin kyakykyawa ne ga lips ɗinsa kamar na mace ƙarami dashi ga yaci launin maroon colour, ga sumar kayi baƙi ƙirin lallausa a ƙwance luf² har zuwa sajensa zuwa gemun, haƙiƙa duk macen data haɗa ido da Junaid bazata taɓa sanin Lokacin da zata shiga wani hali ba, Hafzat ko kaɗan bata ƙaunar Junaid yazo yanda take domin bazata iya juran ganinsa ba, shiyasa idan tana gabansa kanta yake ƙasi bata son ɗagowa ta kalleshi, a yanzun ma bata san lokacin da idonta suka kafu akansa ba, ko ƙibtasu bata yi, wani dogon tunani ta faɗa ciki still idonta akansa, ganin kallon da take masa ne yasa shi mamaki yana tunanin meye dalilin da yasa ta zuba masa na mujiya har haka, hannu yakai saitin idonta yana karkaɗasu yanason ganin shin a hayyacinta take ko sumar zaune tayi, firgit tayi a tsorace ta soma faɗin "innalillahi wayyo Allah mijin Aljanna..." kallonta yayi cikin rashin fahimta yace "kin haukace ne?..." girgiza masa kai tayi tareda cewa "a'ah..." jinjina kai yayi sannan yace "kin iya shayin na'a-na'a?..." dasauri ta ɗaga masa kai alamar ehh, yace "aina kika iya?.." cikin sanyin murya tace "agurin Mommy.." jinjina kai yayi yace "ok kizo ki haɗa mana yanzu" yana kaiwa nan ya tashi yayi ficewarsa, ita kuwa bin bayansa tayi da kallo cikin wani irin yanayi data tsinci kanta a ciki... Around 10 O'clock pm. Sarki Raamud yana nan yanata kai kawo a falo ya kasa zama gaba ɗaya yana cikin damuwa na rashin ganin mommy, sai tambaya yaketa yi "wai shin har yanzu bata dawo bane? kuzo ku kaini asibitin nan naje na dubo ko lafiya tinda safe har zuwa yanzu dare.." Shima Junaid yana zaune akan hannun kujera sai faman ƙiran wayan Ayush yake amma ba'a picking, gaba ɗaya ransa a ɓace yake domin basuyi akan zata kai wannan lokacin bata dawo ba, sai tsaki yake ta ja shi kaɗai.. Ita kuwa Hafzat da Judan suna saman dinnig suna night lunch su biyu, sai jan hankalinta yake da hirar masoya ita kuwa hankalinta yana kan su Junaid, shi yana damuwa akan rashin dawowar Yushert ɗinsa shi kuma Sarki Raamud yana damuwa akan Mommy toh abunda yafi bata mamaki shine "shin meye alaƙar Abbah da Mommy? Bayan ance su ba ma'aurata bane, gaskiya akwai ƙaƙƙarfar alaƙar soyayya a tsakanin mommy da Abbah..." a cewar Hafzat da take ta maganar zuci, duk gidan nan ita kaɗai ta fahimci akwai soyayya a tsakaninsu domin ita take kusa da mommy akoda yaushe inhar tana gida, kuma suna yawan waya, yana daga part ɗinsa itama tana part ɗinta amma haka zasu ɗau lokuta suna waya, wani lokacin kuma sukan haɗu a guest room dake can wani part na gidan, tsararren waje na baƙi idan za'ayi wani ɗan taro! acan suke haɗuwa su sha lovayya, kuma Mommy takan tashi cikin dare misalin ƙarfe 12 ko 1 taje kitchen ta haɗo shayin na'a-na'a takai part ɗin sarki Raamud, saboda shi indai bai tashi yasa wani abu a cikinsa dadaddare ba akwai matsala, hakan yasa mommy take ɗauka masa wannan ɗawainiyar, soyayyarsu suke sha ba tareda kowa yasani ba a cikin gidan, amma ita Hafzat tana bibiye dasu itace CCT ɗinsu, kuma tana yawan ɗaukar wayar mommy da cewar zatayi Game ko kallo haka zata shiga gurin saƙonni taga duk saƙon soyayyar da sarki yake turo mata itama tamayar masa da reply na soyayya, wayan yana hannunta sarki yasha ƙiran mommy amma bata ɗauka saboda bata son su gane cewar ita tasan alaƙar dake tsakaninsu har sai sune suka bayyanar da kansu, tsabar yawan ƙiran da sarki yake yiwa mommy a waya Hafzat har ta riƙe numbersa daman dake number a saved yake an rubuta KING OF KINGS akan numbersa.... Hafzat kallonsu kawai take tana murmushi daga Junaid ɗin har Abbah, kawar da kai tayi ta maida hankalinta kan Judan wanda tin ɗazu yake ta zuba kamar kurna... Bayan wasu mintuna suka ji an turo ƙofar falo da sallama a bakinsu suka shugo, mommy da Ayush a zabure sarki yayo kan mommy yana faɗin "Sarauniya ina kika shiga ne haka gaba ɗaya na shiga damuwa, sauran kaɗan na fita nemanki..." Mommy tayi murmushi tana kallonsa cikin yanayin shagwaɓa tace "kayi haƙuri My king wallahi Ayyuka ne suka riƙeni..." Yace "toh Sarauniya please ki dena kaiwa dare a waje kinji koh?..." tace "Insha Allahu my king zan kiyaye..." cikin farin ciki da annushuwa ya ƙibta mata ido ɗaya, tayi saurin kawar da kanta tana dariya ...." Dasauri Ayush ta waiwayo tana kallonsu cikin mamaki ido kamar zasu faɗo ƙasi jin yanda mommy take ƙiran Abbanta! cikin rashin fahimta ta maimaita sunan da ƙarfi tace "My King kuma?...." a zabure mommy ta ɗago tana kallonta ita sam ta manta cewa akwai mutane a wajen, ganin sarki Raamud yakan sa ta manta da abunda take yi, shima tsabar hankalinsa yana kan mommy kwata-kwata ya sha'afa da cewar akwai mutane a falon, cikin jin kunya yayi saurin barin falon ya koma part ɗinsa, itama mommy bata tsaya bawa Ayush amsa ba ta ratsa ta gefenta ta wuce ɗakinta jiki duk a sanyaye... Gaba ɗaya hankalin Ayush ba ƙaramin tashi yayi ba jin irin maganganun da sukayi irin na masoya, a hankali ta furta "Whatttt can't believe..." Shi kuwa Junaid tin shugowar Ayush yake ta jifanta da wani irin kallo na takaici, sunyi akan idan taje hospital zuwa azahar ko la'asar zata dawo sai gashi har 10 na dare, kuma ba yau ta saba masa haka ba, sai gadarar idan tayi laifi ta soma kuka tana bada haƙuri da magiya amma hakan bashi zaisa gobe ma ta ƙara yin laifin ba, yana cikin huci tazo ta wuce shi ko kallon yanda yake batayi ba haka ta wuce da ƙaton tumbin cikinta kamar zatayi ihu haka take ji tana mamakin yanda mommy da Abbah suka shaƙu har haka... Haka take taka matakalar Benin kamar babu jini a jikinta da haka harta shige bedroom ɗinta, shima Junaid a fusace ya haura yabi bayanta, sai iya Hafzat kawai aka bari ita da Judan har ta fara sakin jikinta dashi... ★★★★★★★ "Yushert! Yushert!! Yushertttt!!! tsabar iskanci kinaji ina ƙiranki amma ko ki kulani bayan laifin da kika yi?.." Ayush tana zaune a bakin gado tana jinsa yanata surutansa amma ko kallonsa batayi ba, kawai maganganun su Mommy ne yake mata yawo aka, dogon tunani ta faɗa ga kuma hawaye shaɓe-shaɓe akan fuskarta, ganin haka yasa Junaid zama a kusa da ita yana faɗin "ke kuma fah? me akayi miki kike kuka?..." murya ciki-ciki tace "Babu komai" Yace "a'a akwai banason ɓoye-ɓoye a lamarina ki fito ki faɗa mun gaskiyar abunda yake faruwa..." cikin nuna rashin son hayaniya da damuwa kamar zata rausa ihu tace "haba Yaya Junaid mekake so nace maka, nace babu komai ba dole ne saika ji ba, please ka ƙyaleni da abunda ke damuna banson hayaniya da damuwa..." cike da mamaki yake binta da wani irin bahagon kallo yace "whattt! Yushert Ni ne hayaniya da damuwa? okay thanks..." cikin takaici ya miƙe tsaye tareda cire jallabiyan jikinsa ya faɗa cikin toilet yayi wanka shaf-shaf sannan ya fito yana ƙamshin sabulu mai daɗin gaske, ya shirya cikin ƙananun kaya three quarter da singlet sannan yazo gaban Ayush kamar bazaiyi magana ba cikin ƙarfin hali yace "tashi mun zan ƙwanta..." tashi tayi tana haɗe rai ta koma kan wata doguwar sofa ta zauna tareda kifa kanta akan gwiwowinta tana rera kuka ciki² Shi kuwa hannu ya miƙa ya kashe hasken ɗakin sannan ya kunna green lamp sai ɗakin ya bada green light mai kyan gaske, ya kwanta tareda jawa kansa mayafi ya lumshe idonsa kamar meyin bacci sai dai yana jinjina maganganun Ayush data yi masa cikin rashin ɗa'a da biyayya sannan yana tunanin shin meya sameta ta shiga damuwa har haka, yana cikin wannan tunanin da haka har bacci ɓarawo yayi awun gaba dashi.... Ayush kasa rintsawa tayi! zuciyarta ba ƙaramin jagwalgwalewa tayi ba, tsananin kishi ne acikin zuciyarta bataso ace mommy da Abbah sun ƙulla soyayya ba domin tana taya mahaifiyarta kishi duk da bata raye, ta shiga kewar mahaifiyarta sosai, kasa haƙuri tayi ta tashi da sauri ta buɗe ƙofar ɗakin ta fice lokacin misalin ƙarfe 12 da rabi ne na dare, kai tsaye falo ta sauƙo cikin rashin sa'a kuwa taga mommy ta fito daga kitchen da flask a hannunta ta nufi part ɗin Abbah, wani irin ƙololuwar baƙin ciki ne ya ziyarci cikin kogon zuciyarta, daƙer ta iya haɗiyar yawu jiki a sanyaye haka ta ƙarasa saukowa falo kai tsaye ɗakin Hafzat ta nufa, tana zuwa ta fara knocking a hankali tana ambatar sunanta, a lokacin cikin sa'a kuwa Hafzat tana kan sallaya ta gama idar da sallar dare tana cikin jan carbi taji kamar Muryar Ayush, cikin mamaki ta taso a hankali tazo dab da bakin ƙofar tace "waye ne?.." tayi maganar domin ta tabbatar ko ita ɗince, cikin kakkarwar murya Ayush tace "nice kiyi sauri ki buɗe mun..." Jin haka yasa Hafzat tayi saurin buɗe mata, Ayush tana shugowa tayi saurin mayar da ƙofar ta rufe saboda bata son mommy tazo ta ganta... Cike da mamaki Hafzat tace "lafiya kuwa Aunty Ayusher? ya naga kamar kuka kike meya faru?.." dasauri Ayush takai yatsanta ɗaya saitin bakinta tana faɗin "shuuuuuu kinayi a hankali kar a jiyo ki kinga dare ne..." ta ƙarasa maganar tareda riƙo hannun Hafzat ta zaunar da ita a bakin gadonta itama ta zauna tana cewa "magana nake so nayi dake.." Hafzat tace. "ina jinki Aunty..." tace "akan mommy nakeso muyi magana naga kinfi kusanci da ita shin meye alaƙar dake tsakanin mommy da Abbah?..." Hafzat bata ji komai aranta ba tace "soyayya mana.." Ayush ta kuma cewa "shin meye hujjarki na cewa haka?.." Anan Hafzat ta ƙwashe komai akan alaƙar dake tsakanin mommy da Abbah ta gayawa Ayush, har zuwansu hira can guess place dake cikin gidan ba tareda kowa ya saniba, daga ƙarshe kuma ta ƙarasa maganar ta da cewa "idan kinason ƙarin bayani kije ki binciki wayar mommy ki shiga WhatsApp ɗinta ko wajen message zakiga an rubuta KING OF KINGS shine number Abba datayi saving dashi zakiga duk wani chatting da sukayi na soyayya abun saiya baki shauƙi...." Ayush kamar wacce aka ɗauke mata wuta haka ƙwaƙwalwarta ya fara juyawa duk ta gama haɗa zufa, zuciyarta ne yake wani irin harbawa da ƙarfin gaske Fattt! Fattt!! Fattt!!! muryarta har harɗewa yake tace "kinsan bansan password ɗin wayarta ba saboda ban taɓa ɗauka ba ki gaya mun yanzu..." Hafzat tace. "amma Aunty Ayusher meyake faruwa ne haka naga gaba ɗaya kin fita hayyacinki?..." tace "kedai faɗamun password ɗinta kawai..." Hafzat ta gaya mata cike da mamaki ganin yanda Ayush ta canza lokaci guda... Dasauri Ayush ta tashi ta fice a ɗakin kamar taza fura sama, ita kuwa Hafzat girgiza kai kawai tayi tareda cewa. "Allah yasa muga Alkhairi toh..." ta tashi taje ta kulle ɗakinta sannan ta dawo ta rage kayan jikinta ta miƙe akan katafaren gadonta nan danan bacci ya ƙwasheta.... Ita kuwa Ayush tana fita daga ɗakin Hafzat kai tsaye ɗakin Mommy ta shige cikin sanɗa har zuwa yanzu mommy bata dawo ba cikin sa'a kuwa ta samu wayarta asaman gado dasauri taje ta ɗauki wayar ta buɗe cikinta daga nan ta shiga waran duba saƙonni, kamar yanda Hafzat ta gaya mata, saƙonnin ta fara karantawa tana kuka tsantsar soyayya kawai suke sha, kuma tana mamakin yanda Abbanta ya iya kalaman soyayya har haka, saida ta kammala karantawa tass har sun gama yanke shawarin yin Aure, Girgiza kai Ayush ta soma yi tareda faɗin "impossible wallahi babu maganar Aure, bazan taɓa barin faruwar haka ba, saboda Ummana bata raye shine za'a ci amanarta? toh bazaiyu ba..." tana maganar zuci tareda ƙoƙarin buɗe WhatsApp ɗinta, jin motsin mutum yana ƙoƙarin shugowa ɗakin ne yasa tayi saurin wurgi da wayar akan gado gudu² sauri² haka ta shige cikin toilet, Mommy ce ta shugo ɗakin cikin farin ciki da annushuwa tana daga tsaye ta zamar da hijabin jikinta ta ajiye shi sannan ta zauna a bakin gado tana tunanin gobe zata sanar da Artaff maganar Aurenta da Sarki Raamud, har sun gama tsaida maganar sadakinta sannan suna tunanin kota ɓangaren yaransu ma basuda matsala, domin zasuyi farin ciki da wannan haɗin shiyasa sukeso suyi bazata, ita kaɗai sai murmushi taketa zabgawa tana murza zoben zinaren yatsanta, juyawa tayi tareda ɗaukar wayanta tana son turawa Artaff saƙon domin bazata iya barin gari ya waye ba tsabar ɗauki, kuma dake hausawa sunce a bari ya huce shi ke zama rabon wani! hakan yasa bazata haƙura zuwa gobe ba, tana buɗe wayar taga tana kan WhatsApp cike da mamaki mommy take kallon wayar, murya a bayyanai tace "WhatsApp kuma? Ni yau kwata² ban hau WhatsApp ba amma taya zan ganni akan WhatsApp alhalin ban shiga ba..." Juyar da wayar ta somayi cike da mamaki gira a haɗe, shiga cikin wayar tayi taga har waran saƙonninta aka duba dake wayar duk yanda mutum ya shiga a wayar za'a iya gani daga baya, itama Hafzat dake tasan kan wayar mommy da zaran tayi shige-shigenta take goge duk yanda ta shiga, ita kuma Ayush ganin babu lokaci ne yasa bata tsaya yin waɗannan goge gogen ba kawai ta ajiye wayar bayan tahau kan WhatsApp... Ayush tana cikin toilet gaba ɗaya harta gaji da tsayuwa ga cikinta yanda yayi mata nauyi sosai bata iya juran tsayuwa, Mommy jikinta ne ya bata cewa akwai wanda ya shugo room ɗinta, ajiye wayar tayi akan drower sannan ta miƙe tsaye tareda nufan hanyar toilet har takai hannunta zata buɗe taji wayarta tana ringing juyawa tayi cikin zumuɗi ta nufi wajen wayar dasauri domin tasan King ɗinta ne, ɗaukar ƙiran tayi tareda karawa a kunne tareda faɗin. "Assalamu alaikum My King..." amsa mata yayi tareda sanar mata cewar takai masa maganin ciwon kai da kuma zazzaɓi domin baya jin daɗin jikinsa jurewa kawai yake bayan mommy babu wanda yasan bashida lafiya.. itama amsa masa tayi cikin rashin jin daɗin rashin lafiyarsa tace "gani nan zuwa my king .." jiki a sanyaye ta fice daga ɗakin kai tsaye medicine room ta nufa zataje ta haɗo masa maganunnuwa... Ayush tana toilet jin wayarda sukayi yasa ta fashewa da kuka ciki² kar a jiyota, jin alamun mommy ta fita yasa itama ta fito tana maida numfashi, haka kawai taji bata ƙaunar soyayyar mommy da Abbah tafison kowa ya Auri nasa a waje can ba lallai sai sun haɗa zumunci ba.... tana cikin wannan tunanin tayi firgit ganin lokaci yana ƙure mata dasauri taje ta buɗe ƙofa tayi ficewarta cikin sanɗa tayi hanyar upstairs dazai sadata da ɗakinsu, kwatsam taji an ƙira sunanta tsayawa tayi da tafiyar domin tasan mommy ce kuma bata son kallonta saboda idan ta tuna irin soyayyar data ga suna sha har kunya take ji da kuma haushi... Mommy tace "keɗin daga ina kike?..." shuru tayi ba amsa har saida mommy ta sake maimaita mata amma still shuru tayi mata, Mommy har zuwa dab da ita tayi tace "Ayushert bai kamata kimun shuru ba, shin ina kika je a wannan daren...? Juyowa Ayush tayi tana kallon mommy fuska a haɗe tace "toh mommy banda abunki ai baza'a rasa wajen zuwa ba..." Mommy tace "A wannan daren?.." cikin ɓacin rai tace "to kema mommy me kikeyi a wannan daren bakiyi bacci ba?..." cike da mamaki mommy take kallon Ayush Lokaci guda kuwa jikinta yayi sanyi domin taga Ayush daga cikin ɗakinta ta fito kuma duk yanda akayi ita ta ɗauki wayar har ta karanta saƙonnin ta da aka tutturo mata na soyayya, jin irin amsuwar da take mata ne yasa ta cewa "Ayush kinada hankali kuwa? shin yakamata kimun irin wannan maganar na rashin ɗa'a?...." Ayush ko kula mommy batayi ba ta cigaba da tafiyarta harta ƙule wa ganin mommy, Mommy ƙirjinta ne ya fara bugawa domin taga rashin nasara a idon Ayush ƙarara bazata yadda da maganar Auren nan ba, mommy jikinta ba ƙaramin sanyi yayi ba haka take jan ƙafa daƙer ta nufi part ɗin sarki Raamud..... Ita kuwa Ayush pillow ta ɗauka ta ƙwanta akan doguwar sofa tana cikin tunani da nazari har bacci ya ɗauketa, A daren yau mommy bata samu yin bacci ba saboda tsananin mamakin maganganun da Ayush tayi mata, kuma tana tunanin halin da zata shiga in har bata Auri sarki Raamud ba, gashi duk abunda Ɓingel take so shi Sarki Raamud yakeyi idan kuma tace bataso to kuwa ko ƙasa da sama zasu haɗe bazaiyi abun ba.... ★★★★★★ Washe gari da safe bayan ta idar da sallar asuba tashi tayi ta fara kai kawo a cikin ɗakin, tana zirga-zirga ta kasa zama har gari yayi wasar a lokacin Junaid ya samu daman dawowa tin fitar sallar asuba ya zauna a masallaci ne domin karatun Alkur'ani, Tana gani ya shugo amma ko kulata baiyi ba balle ya tambayeta dalilin yin zirga-zirgarta, haka ya shige toilet har yayi wanka yayi brush sannan ya fito amma still tana wannan zirga-zirgar, abun yayi matuƙar ɗaure masa kai amma sai dai bazai kulata ba saboda rashin mutuncin data masa jiya, Har cikin ranta tana son sanar masa abunda ke faruwa amma saidai tana fargaban abunda zaiyi mata saboda jiya da fushi ya ƙwana, Shima har ya gama shirye-shiryensa yazo zai fita tayi saurin shige gabansa tana faɗin "Yaya Junaid dan Allah ka tsaya ka saurareni, akwai abunda zan gaya maka ne..." kamar bazaiyi magana ba haka yake kallonta cikin fushi yace "idan baki ban hanya ba sai nayi ƙwallo dake awaran wallahi...." Tace "dan girman Allah kayi haƙuri wallahi ina cikin matsala ne, ka gafarceni mijinaaaa..." Jin ta ambaci girman Allah da kuma fashewa da tayi da kuka yasa yaɗan sauƙo yace "inajinki toh..." dakatar da kukan tayi sannan ta kora masa jawabai akan mommy da Abbah ta ƙarasa maganar da cewa "yanzu haka ma har sun tsayar da maganar Aurensu...." tinda Ayush ta fara magana Junaid ya kafa mata ido jin labarin da take bashi na soyayyar mommy da Abbah zaro da dara-daran idanuwansa yayi cike da mamaki yace "Whatttt! Aure kuma tsakanin mommy da Abbah?..." Ayush ganin kalar reach ɗinsa yasa hankalinta ya kwanta domin tana tunanin zasu haɗu ne su wargaza maganar Auren, Tace "yess of course abunda nake gaya maka gaskiya ne shiyasa tin jiya nake cikin damuwa ai" Lokaci guda Junaid yasau ƙayataccen murmushi na farin ciki tareda faɗin "wow masha Allah, Allah na gode maka daka zaɓawa mahaifiyata mijin da zata Aura, na daɗe ina jiran wannan lokacin burina shine naga mommy tayi Aure itama saboda ba wuce yin Auren tayi ba amma ta kasa yi, nayi mamaki sosai jin mommy tana soyayya abun farin ciki ma wai sarki Abbah zata Aure, zan so Uncle Artaff yaji wannan Albishir...." yana kaiwa nan yayi ficewarsa cikin nuna farin ciki... Ayush kamar ta haɗiyi ranta tsabar ƙololuwar baƙin ciki bata san lokacin data fashe da kuka ba, itama ta fice a ɗakin da haka ta sauƙo falon kai tsaye part ɗin Abbanta ta wuce, tana zuwa kuwa ta samu Abbah yana zaune akan sallaya ga flask ɗin shayi da maganunnuwan da mommy ta kawo masa da daddare, tsayawa tayi ko zama bata samu damar yiba balle gaisuwa ga hawaye yanda yake mata go slow akan fuskarta, Sarki Raamud ganin halinda Ɓingel take cikine yasa ya zabura shima ya miƙe tsaye yana faɗin. "lafiya kuwa Ɓingel mezan gani haka, kinaso ki ƙuntata mun koh? shine dalilin da yasa kika zo kina nuna mun hawayenki alhalin banason ganin hawayenki ko ɗaga indai bana farin ciki ba..." Goge hawayen tayi tana jan zuciya tace "zan daina kuka ne da zaran ka gayamun gaskiya akan soyayyarka da mommy..." Abbah yace "toh banda abunki Ɓingel tinda har kinsan gaskiya ai sake tambaya ma bai taso ba...." Tace "kenam da gaske Aure zakuyi?..." Dasauri ya amsa mata cikin ƙwarin gwiwa domin yana da tabbaci akan Ɓingel ɗinsa cewar zata yadda da maganar, Dasauri ta katse shi da cewa "Tabb ɗin jamm kenam Amanar mahaifiyata za'a ciii?...." tayi maganar cikin ɗaga murya tareda zaro manya-manyan idanuwanta waje tana huci ta kuma cewa "wallahi kar ma a fara wannan zance domin abu ne mai wuya na iya yadda, taya za'ace ka Auri mahaifiyata sannan kuma kazo ka Auri mahaifiyar mijina how comes, dis thing should never do abun baiyi tsari ba gaskiya wannan ai cin amana ne ƙarara da kuma rashin karaaa..." Abbah gaba ɗaya shima jikinsa ya mutu yayi sanyi wani irin zazzaɓi ne ya ƙara rufoshi jin Ɓingel bata yadda da maganar Aurensa da mommy ba, cikin harɗewar murya yace "Ɓingel shin mekike faɗa hakane? Kada kice zakiyi haka domin zaki cutar da zuciyata ne, na kamu da tsananin son Hajia Fateema kar kimun haka dan Allah...." Itama tana kuka tareda faɗin "nima Abbah zaka cutar da zuciyata inhar ka Auri mommy domin bansan da wani ido zan rinƙa kallonta ba, wai ace surkuwata ta zama matar ubana? bantaɓa ji ba ko a Film, toh ma Abbah dole ne sai kayi Auren ? ka zauna mana haka mezai sameka ..." Yace "Ɓingel koda banyi Aure dan kaina ba dole zanyi Aure dan masarauta na domin babu Sarkin da yake zama babu matar Aure, kuma kina maganar Mommy surkuwarki ce shin Addini ya haramta na Aureta ne? matar ɗan uwana ne pah dan na Aureta saboda bashida rai saiya zamo laifi?...." Cikin yanayin damuwa tace "Ni kawai banasooo! na dantse alaƙar soyayyarku babu maganar Aure kuma idan har anason zaman lafiyata a gidan nan...." Kafin Abbah ya ƙara cewa wani abu harta juya zata bar ɗakin tayi kucuɓuss da mommy a bakin ƙofar ɗakin tana tsaye duk taji maganganun Ayush daga A har Z, Ayush burki tayi itama ta tsaya tana kallon Mommy.... Shi kuma Junaid yana can ɗakin mommy yana jiranta akan ya nuna mata takardar ƙarin matsayisa zuwa General a ƙasar california, sannan kuma sai su tattauna game da maganar Aurenta da Sarki Raamud kafin a sanarwa Uncle Artaff...... *DAN ALLAH NIMA INA BUƘATAR COMMENTS ƊINKU 🙏🙏🙏 INASON GANIN ZAFAFAN COMMENTS....* 𝑡𝑦𝑝𝑖𝑛𝑔✍️ 𝗠𝗔𝗧𝗔𝗥 𝗗𝗔𝗠𝗨𝗦𝗔 the wife of a tiger🐅🐅🐅🐅 𝙼𝚊𝚕𝚕𝚊𝚔𝚒𝚗 𝙰𝚜𝚖𝚎𝚎𝚝𝚊𝚑 ✍️✍️ 𝙿𝚊𝚒𝚍 𝚋𝚘𝚘𝚔 𝚌𝚊𝚕𝚕 𝚘𝚛 𝚠𝚑𝚊𝚝𝚜𝙰𝚙𝚙 09065443871 *💫💫{{N W A}}💫💫* Book two C̶h̶a̶p̶t̶e̶r̶ 71 to 75 Mommy tana kuka tabar ɗakin sarki Raamud jin abunda Ayush take faɗi, kai tsaye ɗakinta ta nufa tana shiga ta tarar da Junaid yana zaune a bakin gadon yana jiran shugowarta, ganinsa yasa tayi saurin goge hawayen fuskarta cikin ƙarfin hali tace "my son yadai na ganka yau kamar kana cikin farin ciki..." da murmushi ƙwance saman fuskarsa ya ɗago yana kallonta lokaci guda kuma ya haɗe ransa ganin yanda idon mommy yayi ja alamar tayi kuka sosai, dasauri ya miƙe tsaye ya riƙo hannunta tareda faɗin "why Mom, meyasa kike kuka ba tareda nasan dalili ba..." Mommy daƙer take ƙwaƙulo murmushi saboda kar Junaid ya sakata a gaba da wasu tambayoyinsa, tace "babu komai ka kwantar da hankalinka ba wani abu bane.." Junaid ƙura mata ido yayi tareda ɗago hannunsa ɗaya yana goge mata guntun hawayen da yake shirin gangaro mata, cikin sassanyar murya yace "Mom zauna kinji koh" ya zaunar da ita a bakin gadonta shima ya zauna yana fuskantar ta kamar zaiyi kuka haka yake ji saboda ya tsani ganin hawayen mommy ko kaɗan, shiyasa yake ƙoƙarin mata duk abunda takeso indai bana cutarwa bane, yace "Mom bakya kuka akan abu saidai idan yakai maƙura, dan Allah kar ki ɓoye mun Mom..." Mommy kamar bazata sanar masa ba kawai taji cewar gwara ta gaya masa duk halin da ake ciki, tana kuka ta soma kora masa duk abubuwan da suke wakana a tsakaninta da sarki Raamud, Jinjina kai Junaid yayi yace "Okay shine dalilin da yasa Yushert tayi mun wulaƙanci jiya? okay I will teach her a lesson..." a firgice ya miƙe tsaye zai fita mommy tayi saurin riƙo hannunsa tareda cemasa "yanzun ina zakaje " yana huci yace "Mom haƙuri na yazo ƙarshe, bazan iya juran wulaƙancin Yushert ba, yanzu saboda iskanci irin nata duk rashin mutuncin da take mun ina shanyewa bai isaba har saita taɓo mun mahaifiyata, to wallahi mommy yau babu abunda zai hana na saki Yushert ko kuma na mata ɗan iskan duka..." Mommy cikin lallami take roƙonsa tace "a'ah baza aje wannan gacin ba, kayi haƙuri komai zai zo cikin sauƙi, mu bita a hankali yarinta ke damunta..." Junaid yana tsaye fuska a haɗe tsananin ɓacin rai ne ya bayyana akan fuskarsa sam baiji daɗin abunda Ayush tayiwa mommy da Abbah ba ta mayarsu kamar ƙananun yara, Bai ankara ba yaji mommy ta jawo hannunsa tana cewa "zo ka zauna ka sanar mun abun farin cikin dake tafe dakai my son..." jiki a sanyaye ya zauna sai faman tsuka yake tayi daƙer ya iya motsa hannunsa ya miƙawa mommy takardar ƙarin matsayinsa, karɓa tayi tana faɗin "wannan fah..." buɗe takardar tayi ta soma karantawa lokaci guda ta miƙe tsaye dasauri tana zazzaro ido waje baki a sake ta juyo tana kallon Junaid dake zaune shima zuba mata ido yayi ganin yanda ta kasa yin magana tsabar farin cikin data shiga, lokaci guda ta durƙusa da gwiwowinta ƙasi ta ɗaga hannayenta sama tana faɗin "Alhamdulillah! Alhamdulillah!! Alhamdulillah!!! Allah mun gode maka...." kasa ƙarisa maganar tayi takai hannu ta rungumo Junaid tareda fashewa da kukan farin ciki, Junaid shima rungumar momminsa yayi yana faɗin "it's okay my mom bana son ganin hawayenki na gaya miki koh"... ɗagowa tayi tana kallonsa cikin farin ciki tace "my son kukan farin ciki nake yi, sakamakon wannan gaba ɗaya Allah ya yaye mun duk wani ƙunci da nake ciki..." Murmushi yayi sannan yace "Mom ki daina saka damuwa aranki, nayi miki Alƙawari duk abunda kike so a duniyan nan koda zan rasa rayuwata zanyi miki shi!.." Mommy tace "Insha Allahu babu abunda zaisa ka rasa rayuwarka my son..." jinjina kai yayi sannan ya kuma cewa "yanzun gaya mun kina son Sarki har cikin zuciyarki kuma zaki Aure shi?..." Mommy tace "meyasa kamun wannan tambayar?.." haɗe tafukan hannunsu yayi idonsa akan mommy yace "please tell me..." ya ƙarasa maganar kamar irin shagwaɓaɓɓun nan, mommy kamar zata fashe da kuka tace "har mun tsayar da maganar mu cikin sauƙi ina tunanin zakuyi farin cikin hakan shiyasa muka yanke cewar bazata zamuyi muku, toh sai akayi rashin sa'a Ayushert bata son Auren bansan dalili ba shiyasa yanzu zan yanke hukuncin warware maganar Auren banason ayi abu cikin ɓacin rai kaga mu ba yara ba balle..." Girgiza kai Junaid yayi sannan yace "kar ku damu Mom Aure kamar anyi shi ne, kar ku yadda yarinya ƙarama ta juyar da ƙwaƙwalwarku, shin ita take da iko daku ne? ko kuma ita ta haifeku? ki kwantar da hankalinki komai zai zo cikin sauƙi Okay..." Mommy ta jinjina kai tana murmushi tace "thank you my beautiful Son..." ɗagowa yayi ya sumbaci Mom akan goshinta tareda faɗin "ina ji dake my Mom, take care..." ya miƙe zai fita tayi saurin cewa "ya naga kana tafiya jiki ba ƙwari kodai yunwa? ooooh bari nayi saurin shiga kitchen banson barin yarona da yunwa ga itama Ayushert ciki ya tsufa dole nasan tana jin yunwa, ta ƙarisa maganar tareda ficewa daga cikin room ɗin, a tare suka fito falo suna ɗan hirarsu mommy ta hango Hafzat sai faman shirya kuloli take akan dinning daman tare suke shiga kitchen, cikin sakin fuska mommy tace "Hafzat kar dai ace har kin gama abincin breakfast?.." Hafzat tace "na gama komai Mommy daman ai zuwa yanzu kam yakamata ace kin huta tinda ina gidan zan iya yin ko wani aiki..." Mommy tace "a'a bazan iya bar miki komai kiyi ba, kema kina buƙatar hutawa..." tana dariya tace "mommy kar ki samu damuwa Ni aiki ba komai bane a waraina saboda na rigada na saba baya bani wahala kasancewa ta a gidan talakawa na fito dole na motsa jikina, in banyi aiki ba jikina ciwo yake..." Mommy cikin farin ciki take kallon Hafzat haka kawai yarinyar take burgeta, ga bata da matsala tace "shikenam Shalele nah Allah yayi miki Albarka..." Hafzat cikin nuna farin ciki ta amsa da"Ameen..." Duk maganganun da suke yi Junaid yana zaune yana jinsu ɗagowa yayi ya kalli gurin da Hafzat take yace "Ni ba'a kammala bane?..." tace "an gama Uncle.." miƙewa yayi ya nufi wajen domin ba ƙaramin yunwa yake ji ba, tin jiya da rana bai ci komai ba, mommy tace "yauwa duk kije kowa kice yazo an kammala breakfast su fito, kije ɗakin Judan shima kice yazo ...". Hafzat ta amsa da "toh mommy" dake indai za'ayi breakfast ko lunch na rana dana dare duk a tare suke zama a dinning suci domin ƙarfafa zumunci, daman ance cin abinci a tare da mutane yakan ƙara ƙarfi zumunci a tsakani, Hafzat part ɗin Abbah ta fara zuwa ta sanar masa cewa an kammala breakfast bayan ta gaishe shi, ta fito ta haura upstairs taje ta ɗakin Ayush tana knocking daga ciki tace "yesss..". Hafzat ta sanar mata cewa tazo suyi breakfast, Ayush shuru tayi kamar baza tayi magana ba daga ƙarshe tace "bazan fita ba yanzu kije ki kawo mun yau Ni kaɗai zanci..." cike da mamaki Hafzat tabi ƙofar da kallo a cikin ranta tace "lallai Aunty Ayusher baki so a zauna lafiya ba, tin jiya kina abu kamar wata mai Aljanu, shikenam..." ta juya tayi tafiyarta tana sauƙa falo ta wuce part ɗin da aka ajiye Judan taje tana knocking ƙofar ɗakinsa ba jumawa sai gashi ya buɗe yana sanye da jallabiya a jikinsa da murmushi akan fuskarsa yace "shugo mana.." tace "a'a daman cewa akayi nazo nace an kammala breakfast kazo aci dakai..." idonsa akan kyakykyawar fuskarta yace. "okay am coming.." juyawa tayi zata tafi yayi saurin riƙo hannunta dasauri ta juyo tana kallonsa, a hankali yake motsi da lips ɗinsa yace "you are a beautiful girl, please do you love me?...". kallonsa kawai take tama rasa mezata ce masa sai ƙoƙarin zamar da hannunta take.. shi kuwa ya riƙe hannun sosai yanda bazata iya ƙwata ba, ya kuma cewa "Afzee ki soni dan Allah zan riƙe ki da gaskiya ..." Hafzat tsayawa tayi ta zuba masa ido cikin ƙanƙanin lokaci kuma ta tintsire da dariya jin sunan da ya ƙirata wai Afzee, ɗagowa tayi tace "Ni ka sake ni..." Dariyarta ba ƙaramin burgeshi tayi ba yace "meya baki dariya?..." ya ƙarasa maganar tareda sakin hannunta kafin ya kuma cewa wani abu har ta ruga da gudu tabar wajen... tana zuwa gurin dinning ta tarar da Abbah har ya fito yana zaune akusa da mommy shi kuwa Junaid yana ta ɗayan ɓangaren yana fuskantar su Mommy shima kujeru biyu ne a wajen nashi dana Ayush, sai kuma kujera ɗaya ta gefe itace wanda Hafzat ta zauna a gurin tana fuskantar kujerar da Judan zai zo ya zauna, Hafzat tana zama saiga Judan ya iso wajen shima duk ya gaishesu tareda zama, Mommy ce ta kalli Hafzat tace "ina kuma Ayush?..." sai a lokacin ta tuno da abunda Ayush tace mata tace "Ohhhh na manta ta ce bazata samu damar fitowa ba wai nakai mata can ɗakinta..." ta ƙarasa maganar tareda miƙewa tsaye tana ƙoƙarin ɗaukar flask zata kai mata, Junaid a fusace ya miƙe tsaye tareda faɗin "dakata ke ajiye kular ku fara cin abincin ina zuwa..." yabar wajen dasauri ya haura upstairs yana zuwa ya tura ɗakin yaji a ƙarƙame nan ya fara buga ƙofar, tana daga ciki tace "wai waye ne kam?..." "Kizo ki buɗe mun..." jin muryar Junaid yasa ta taso tazo ta buɗe masa fuska ba yabo ba fallasa har zata juya ta koma ciki yayi saurin damƙar hannunta tareda juyar da ita suna fuskantar juna cikin ɓacin rai yace "meyasa bazaki zo ayi breakfast ba?..." kawar da kai tayi gefe tace "haka kawai" in short answer binta yake da kallo yace "haka kawai? shin kin taɓa yin haka?..." ta finciki hannunta daga riƙon da yayi mata tace "ha'a yau banyi niyar ci da mutane ba ko ana dole ne, nace a kawo mun nan idan kuma baza'a kawo ba shikenam zan zauna da yunwa duk ba abun damuwa bane..." ta juya kafin ta ankara ya cabki wuyanta ya mannata da jikin gini a ruɗe taɗan saki ƙara tana faɗin "wayyo Allah cikinaaa..." Idonsa yakai saitin nata sai faman zazzaro mata su yake yana huci yace "ki kalli cikin eyes ɗina kin rigada kinsan halina, na fahimci akwai tsutsotsi acikin ƙwaƙwalwarki to kuwa zan cire miki su ɗaya bayan ɗaya, Idan kina ganin wannan ƙaton cikin nakin ne zaisa na ƙyale ki toh kuwa tunaninki baizo daidai ba domin Junaid yakan makance ne a yayin da zuciyarsa ke tafarfasa, idan kika ce zaki ƙona mun rai wallahi zan iya wurgi dake ta window inyaso naga abunda zai faru, useless girl wanda baki san wanda yake miki amfani ba, kuma daga yau idan na sake ganin mahaifiyata ta zubar da hawaye ata sanadiyarki to kiyi kuka da kanki domin a ranar zan warware igiyar Auren mu kuma na hukunta ki...." ya tsayar da maganar yana huci idanuwansa acikin nata yanda ya ɗago da haɓarta sama suna kallon juna, Jikinta ne yahau ɓari tana son sauƙar da kanta ƙasi domin bazata iya juran ganin cikin eyes ɗinsa ba, tsananin tsoro da firgici ne zalla aciki idanuwansa, ta kasa sunkuyar da kanta sakamakon haɓarta daya riƙe ga hawaye duk ya wanke mata fuska, gwala-gwalan idanuwanta sunyi ja hatta fuskarta ma ya koma jaa abunka da farar mace, cikin zuciyarta kuwa kamar wanda ake lugujen hatsi tsabar bugawar da yake yi, leɓɓen bakinta kamar wanda ake jona musu shocking sai kakkarwa suke, yana jin yanda haƙwaranta suke dukan juna, Gani take kamar zai koma mata tiger ne, firgicin da take gani a lokacin da yake komawa Damisa shine yake shirin bayyana a halin yanzu, batayi tunanin haka ba, tayi zaton zai komo mai sauƙin kai ne kuma zai iya juran duk abubuwan da take masa sai gashi ya kasa sauyawa daga tiger zuwa Junaid, bata san lokacin da ya saki haɓarta ba ya riƙo hannayenta ya ɗagesu sama yana manne dasu a jikin bango, still fuskar nan kamar zai rikiɗe zuwa tiger, idonta acikin nashi ta kasa ɗagesu kamar wacce tayi sumar tsaye tana cikin tunane tunane taji ya katseta da cewa "ki dena mun kakkarwa da lips ɗinki..." tana so ta dakatar da faruwar hakan amma ta kasa saima ƙara kakkarwa suke, ido ta zaro tana kallonsa ganin ta kasa tsayar da kakkarwar, "Nace ki daina mun kakkarwa da lips ɗinki..." ya ƙara maimaita mata tareda ƙara fusata, still lips ɗinta kamar wanda ake ƙara musu gudu gaba ɗaya jikinta kamar ana jona mata shocking, Ganin taƙi denawa ne yasa ya daka mata wani irin gigitaccen tsawa har saida ta saki fitsari a jiki tareda sumewa ta faɗa jikinsa, ga tumbin cikinta yanda ya tokare shi babu halin da zasu haɗe gaba ɗaya, ɗago kanta yayi daga jikinsa ya jinginar da ita a jikin gini ido a lumshe, yanda ya jinginar da ita haka yabar wajen yaje ya ɗauki bottle na ruwa a cikin wani ɗan ƙaramin frig a ɗakin ya nufo warenta tareda buɗe murfin gorar ya tsiyayi ruwan sanyi ya watsa mata akan fuska, a firgice numfashi ta ya dawo mata tayi gefe zata faɗi yayi saurin riƙota ya maido da ita yanda take a tsayen, a ruɗe ta haɗe hannayenta biyu tana roƙonsa cikin kuka take cewa "dan Allah kayi haƙuri wallahi wallahi bazan ƙara ba, kayi mun afuwa..." tana kuka tana masa magiya, still lips ɗinta bai daina kakkarwa ba, Idonsa akan lips ɗinta wanda yaketa kakkarwa tana fizgar numfashi sama-sama, tana yin maganar cikin ƙiƙƙina! Yace "kin kasa daina sheckin da lips ɗinki koh?..." "Wallahi wallahi na kasa kayi mun rai, idan kana gabana a haka bazan iya denawa baaa..." ta ƙarasa maganar tana kuka, Hannu yasa ya cabko sumar kanta ta baya ya ƙara matso da ita jikinsa cikin ɓacin rai yana zazzaro mata dara-daran idanuwansa yace "kika ce bazaki iya baaaa..." buɗe baki tayi zatayi magana cikin kuka yayi saurin haɗe musu baki guri ɗaya, shuru tayi sakamakon haɗe musu baki da yayi cikin salonsa ya kamo harshenta ya soma socking a hankali yana shafar sumar kanta, yaga ba ƙaramin tsorita tayi ba kuma ba'a son mai ciki ta kasance cikin fargaba da tsoro hakan yana haifar da matsala a jariri tin kafin yazo duniya, bazai iya barin ta a cikin wannan firgicin ba shiyasa yayi mata haka saboda hankalinta ya kwanta, saida ya ɗau mintina yana mata wasa da baki kafin itama ta soma mayar masa da martani, tayi niyar bazata biye mishi ba amma hakan ya gagara bazata iya jura ba, sun daɗe a haka kafin ya kawar da kansa idonsa akanta, ita kuma ƙwantar da kanta tayi saman faffaɗar ƙirjinsa ido a lumshe, hannu yasa ya ɗagata suka nufi toilet zai wanke mata jiki saboda fitsarin datayi a jikinta, bayan ya kammala ya fito da ita ya sauya mata kaya, sannan ya zuba ruwa akan fitsarin ya juya yana kallon ta yace "kin ɓata mun carpet dole yau za'a fitar dashi a saka wani...." yana rufe baki sai sukayi ana knocking ƙofar ɗakinsu, fuska a haɗe yace "waye?..." Tace "nice uncle dama mommy ce tace a kawo muku abincin..." yace "ki koma da abincin kan dinning zata zo ta ci, banason shirme .." ya kalli yanda Ayush take zaune a bakin gado yace "ki taso muje..." jiki a sanyaye ta tashi kallo ɗaya tayi mishi ta sunkuyar da kanta ƙasi da haka suka fice suka nufi falon... Suna sauƙa falo suka tarar da kowa a zaune a kujerar falo ga Uncle Artaff shima yazo da matarsa Aunty Zainab da yaransa su uku, Junaid yana ganinsu ya fara sakin murmushi domin shi yanzu kamar bazai mutu ba tsabar farin cikin cikar ahalin mahaifinsa, gaba ɗaya gaggaisawa suka shiga yi ga mommy ga sarki Raamud suna zaune a kujera 3 seater saita ɗayan kujera kuma Judan ne sai kuma Hafzat dake zaune a ƙasan carpet, shima Junaid kujera ya samu ya zauna tareda faɗin "yanzu nake shirin zuwa muku ai..." Uncle Artaff yace "wallahi kuwa ɗazu maimartaba ya ƙirani ai yake cewa akwai matsala agidan nan duk ya sanar mun abunda ke faruwa na Aurensa da Hajia...." Mommy kallon sarki Raamud tayi ita sam bata san har ya sanar musu bama, Junaid yayi murmushi kansa a sunkuye, Ita kuwa Ayush dinning ta wuce ta zauna tareda tsiyayan ruwan tea duk tana jin abubuwan da suke faɗi, ji tayi Junaid yace "Ni wallahi so nake ace zuwa gobe an ɗaura Auren mommy da Abbah..." dasauri ta burtsar da shayin data kurɓa tareda zaro manya-manyan idanuwanta tana kallon yanda Junaid yake, Mommy tace "a'ah yayi sauri ai My son" Junaid yace "ohh soyayyar wajen bata ƙare ba kenam?..." Duk suka tintsire da dariya suna wasa da dariya a tsakaninsu, Sarki Raamud yace "daman matsalar akan Ɓingel ɗina ne bansan meye matsalar ta ba, kwata² bata son Auren nan, shine nake so a bincika mun ita ko akwai wani abu aranta ne..." Junaid yayi saurin cewa "meye abunda yake ran natan wanda zai hana Aurenku? kawai ku rabu da ita daman zaman da tayi a daji Aljanu sun shafeta shiyasa kuka ga tana wasu abubuwa kamar mahaukaciya..." Mommy tace. "Aljanu kuma?..." yace "sosai ma Aljanu ne na masifa acikin wannan dajin, nima na gansu da idona balle ita da tayi watannu a wajensu, kuma akwai wani malamin daya tabbatar mun da cewa Yushert tana da Aljanu na rashin ji da fahimta, sun ɗanso su taɓa mata ƙwaƙwalwa, kawai kar ku biye mata..." ya ƙarasa maganar tareda kallon wajen da take, itama ido ta zazzaro tana masa wani irin kallo, acikin ranta kuwa cewa take "tabb ɗin amma Yaya Junaid ba ƙaramin raina mun wayo yayi ba wallahi, kenam zaisa su rinƙa mun kallon mahaukaciya alhalin babu komai a jikina, toh wallahi Auren nan bazan bari ayi ba, zan hura wa Abbana wuta ne har saiya haƙura da maganar Auren aikin banza kawai, yaushe aka taɓa yin haka surkuwarka ta zamo matar ubanka mttssw..." Uncle Artaff yace "toh amma meyasa baka sanar mana haka ba tin abaya? ai da mun tashi tsaye akanta..." girgiza kai Junaid yayi sannan yace "yanzu ne abubuwan suka fara bayyana..." Mommy tace "Allah sarki my daughter insha Allahu za'a nema mata magani, ga zaman da tayi a prison Sam banji daɗin haka ba, shiyasa gaba ɗaya nake ganinta a fizge..." Sarki Raamud kawai yana jinsu ne amma yasan Ɓingel ɗinsa bata da wasu Aljanu, domin tin lokacin da aka haifeta yayi mata wani sihirin da ba wani Aljani ko Aljanar da zata raɓeta ko ta cutar da ita ko kuma ta tsoritar da ita, duk Aljanun da sukayi gigin raɓan jikinta zasu iya ƙonewa, wannan sihirin yana nan a jikinta kuma haka shima kansa, kuma duk mai Aljanu indai Sarki Raamud ya ganta saiya san tanada akwai, saboda ya zauna dasu kuma yanada alaƙa sosai dasu, kamar ita Hafzat yana ganinta yasan tanada Aljanu akanta amma saidai Aljanunta ba masu cutarwa bane shiyasa baiyi magana akansu ba, Aljanunta masu yawan ibada ne haka kawai tana cikin bacci zasu yanke mata baccin ta tashi tayo alwala taita salloli, kuma lokacin sallah yana yi bata barin lokacin ya wuce zata tashi tayi ga yawan azumi da tasbihi kuma intaji anyi karatun Alkur'ani sau ɗaya a gabanta zata riƙe a ƙwaƙwalwarta yanzu sauƙar Alkur'ani Hafzat sau biyar, tayi na waresh sannan tayi na hafs, shu'uba, ƙalun, warshu, durii, susii, ƙumbul, bazzii, ibni kasiir, duk tayi sauƙa akan su ... Ayush kifar da kanta tayi akan table tana kuka jin yanda ake ta janyo mata Aljanu an ɗauketa mahaukaciya, tana cikin kukan taji Abbanta yace "Ɓingel Abba zo mana..." tana jinsa amma ko motsi batayi ba, ya sake ƙiranta taƙi amsawa nan ma! Junaid ya juyo yana kallonta cikin ɓacin rai yace "ke ba magana ake miki ba?..." ɗagowa tayi tana kuka ta taso kamar mai tambayar ƙasa da haka ta ƙaraso cikin falon fuska duk tayi ja da idanuwanta, tsayawa tayi ta kasa zama saida Abbah ya sake yi mata magana yana ƙiranta cikin lallami yace "zo ki zauna anan maza Ɓingel Abbah..." zuwa gurinsa tayi ya riƙo hannunta ya zaunar da ita a tsakiyar su shi da mommy, tallafo fuskar Ayush mommy tayi ta juyo da ita suna fuskantar juna tace "Ayush ki dubi fuskarki yanda duk ta kokkoɗe lokaci guda? dan Allah ki sanar mana meyake faruwa dake, idan bakya son Auren nan ki sanar mana mu zamu san yanda zamuyi, muna buƙatar ganin farin cikin ki..." kuka Ayush take ta juyar da kanta gefe gaba ɗaya ta rasa meyake mata daɗi a ranta, Uncle Artaff ne shima yayi mata magana yace "Ayshert ki faɗa mana meyake damunki ne haka?.." Junaid yace "ku rabu da ita kawai.." Uncle Artaff yace "a'a ka barmu da ita kawai dole musan ƙwaƙƙwaran hujjarta na cewa bata son Auren ." Ayush hararar Junaid tayi tareda cewa "wai kai Uba nane kam.." ciki-ciki tayi maganar ba tareda sunji abunda tace ba saidai sunji kamar tana gunaguni, Junaid kallonta yayi cikin rashin fahimta yace "me kika ce?.." duk babu wanda yaji abunda tace sai mommy da Abbah dake a gefe da gefenta suke, murmushi mommy tayi tareda sunkuyar da kanta tana murza zoben yatsanta, Uncle Artaff yace "kaga Junaid ya isa haka, yakamata kana sanyaya zuciyarka kaga matarka ce kar ka shiga hakkinta..." sannan ya dawo da ganinsa kan Ayush ya kuma cewa "ehen muna jinki Ayshert..." tana motsi da lips ɗinta kamar mai yin magana tace "babu komai.." Hafzat tana zaune a ƙasan carpet tana tunanin dalilin da yasa Ayush bata son Auren nan kuma alhalin abun farin ciki ne... shi kuwa Judan tashi yayi yabar falon ganin tattaunawa ne akan ahalin gidan bai shafeshi ba, bayan ya bar wajen itama Hafzat tashi tayi zata tafi kasancewar maganar manya ne, har ta fara tafiya mommy ta ƙirata tareda faɗin "Judan ya manta earpiece ɗinshi ɗauka ki kai masa, saida Hafzat taji rass a zuciyarta saboda tasan naci irin na Judan yanzu saiyace zai tsayar da ita, ɗauka tayi jiki a sanyaye ta nufi part ɗinsa... itama Aunty Zainab tura yaranta tayi akan suje suyi wasa.. Uncle Artaff yace "Ayshert magana muke miki meyasa bakya son Hajia Fateema ta raɓi mahaifinki? Alhali ta temake ki a rayuwa ta baki gata, ta nuna miki soyayyar gaskiya, ta riƙe ki tamkar mahaifiyarki, inda ace cutar dake zatayi toh da tin farko bata kawoki gidanta ta zamar dake mutum ba, da farko kinsa musu wuta a gida kuma kinsan Hajia Fateema tana gidan kinyi niyar ki ƙonata Allah kuma ya kawo mata agaji, idan ace wata ce da tinin kun raba hanya domin zata ɗauka ke maƙiyiyarta ce amma mai? saita danne hakan a zuciyarta ta gagara cireki a ranta kuma ta cigaba da zama dake, ta ɗauke ki tamkar ɗiyar data haifa a cikinta amma ke baki ɗauketa a matsayin mahaifiya ba, ganan yaronta shi da yake ganin mahaifiyarsa ce ai koda wasa bazai taɓa gigin cutar da ita ba, kinzo kinyi nadama daga baya munji mun karɓi tuban ki amma meyasa yanzu kuma abun ƙaruwa da farin ciki yazo mata kuma kike mata ƙyashin samunsa ko hassada da baƙin hali! kenam kin nuna mata cewa ke butulu ce kenam? kuma a hakan mijinki zaiso ki bayan yasan bakya son mahaifiyarsa? Ehhh...." ya ƙarasa maganar cikin fushi yana zazzaro mata Ido domin Uncle Artaff bai taɓa shiga ɓacin rai irin na yau ba, koda a baya datasa wuta a gidansu ma ransa ya sosu amma bai nuna mata ba saboda a lokacin basu san alaƙar da ke tsakaninsu ba, Daman can Uncle Artaff (malam Lawan) ya fi su zafin rai sosai kuma zai fito ya gayawa mutum magana koda ran mutum zai ɓaci, mai sanyin zuciya daman Máahmud ne baban Junaid shi wannan mai haƙuri kenam ko kaɗan bashida matsala, kuma ba'a taɓa samun wanda akace yayi faɗa dashi ba, Sarki Raamud kuma shi saidai mugunta, duk wani aikin mugunta ya iya shi tin yana yaro, amma yanzu kam Masha Allah ya daina wannan muguntar nashin... Ayush fashewa tayi da matsanancin kuka jin yanda Uncle Artaff yake gaya mata maganganu, daman da farkon yana sassauta mata ne saboda baƙin fuskokin da suke wajen bayaso yayi magana awajensu da kuma yaransa tinda yanzu sun tashi sun tafi iya yasu-yasune hakan yasa ya buɗe mata wuta, Sarki Raamud shima sam baiji daɗin maganganun da ya gayawa Ɓingel ba, kawai dai ya sharar ne, jin tayi shuru sai faman kuka take tayi yasa Uncle Artaff ya darara mata tsawa tareda faɗin "magana nake miki Ayshert yakamata ki kawo karshen ƙudire-ƙudiren da kike yi akan wannan Ahali biyu da kika zamo musu ƙarfen ƙafa, banda mugunta babu abunda kika iya kenam? wani irin baƙar zuciya gareki ne? kodai muguntar da mahaifinki yayi a baya ne ya dawo kanki?...." Sarki Raamud gaba ɗaya zuciyarsa tafasa take da jin kalaman Artaff, mommy ce ta dakatar dashi tana bashi haƙuri da cewa "kayi haƙuri Malam, mu saurara muji daga bakinta..." ta dafa kafaɗar Ayush tace "kiyi haƙuri Daughter kinji yanzu gaya mana abunda yake zuciyarki..." Ayush ta gagara dakatar da kukan da ya kuɓuto mata domin anyi mata bahagon fassara da mummunan zargi akan wai bata son Mommy..." daƙer ta iya dakatar da kukan tace "Ni Allah yaga zuciyata mommy abun alfahari nane, koda wasa ban taɓa jin haushin mommy ko kaɗan ba acikin zuciyata, mommy tamun halacci a rayuwata wanda har ƙarshen numfashina bazan taɓa mantawa baaa..." tana kuka gaba ɗaya ta fita hayyacinta, eyes ɗinta sun zama jajawur har dishi-dishi take gani tsabar kukan data sha, ta cigaba da cewa "nasan kuna jin haushi na amma kuyi haƙuri idan na mutu shikenam, ina roƙon Allah yasa wannan cikin dake jikina ya zamo ajali na da zaran na haifa muku Baby...". ta ƙarasa maganar tana kallon Junaid wanda kansa yake kallon ƙasi tin lokacinda uncle Artaff ya soma magana... lumshe idonta tayi ta matso hawayen da suka kwanta mata akan idonta tana jan numfashi tace "Indai haka halina yake nima nayi Allah wadar da kaina, bansan meye butulci ba saboda tinda mahaifiyata ta haifeni babu wanda ya taɓa temako na sai mommy, itace macen farko dana buɗe idona na ganta a gabana a matsayin bare kuma har ta temakeni ta mayar dani mutum, Bansan meyake damuna ba, haka kawai sai in yanke hukunci cikin rashin tunani da hankali, idan akace nayi gabas ni kuma sai nayi yamma, wallahi bansan me yake damuna baaa, bansan meyasa banason Auren mommy da Abbah ba, haka kawai nake jin ƙunci a zuciyata..." Uncle Artaff kallon sarki Raamud yayi sannan yace "akwai wani abu wanda yake tattare da ɗiyarka kuma abun daga sashinka ya fito..." sarki Raamud kallon Artaff yayi cikin rashin fahimta yace "nidai nasan Ɓingel batada Aljanu..." Uncle Artaff yace "kai wannan kawai ka sani amma bakasan abunda suka ajiye maka ba..." girgiza kai sarki Raamud yayi kwata-kwata bai fahimci abunda Artaf yake nufi ba, Uncle Artaff ne ya kalli matarsa Zainab yace mata "a cikin jakar hannunki akwai wani abu a leda ki miƙo mun...". kamar yanda yace haka kuwa tayi sannan ya ce wa Ayush tazo gabansa ta zauna... itama hakan tayi jiki a sanyaye ba ƙwari, durƙusawa tayi a gabansa tana hawaye, wani ɗan ƙaramin ƙwalba ya ciro ya buɗe murfin sannan ya tsiyayi wani farin Ruwa yace mata "buɗe bakin ki..." ta buɗe bakinta cikin fargaba da tsoro haka ya bata wannan ruwan sannan ya mulmulka mata akan goshinta, yace "buɗe cikin ki.." haka ta ɗage rigarta ya shafa mata wannan ruwan.. Ita dai ta gagara ganewa duk wannan na menene, lokaci guda ta fara jin wani irin zafi da raɗaɗi ajikinta, kayinta ne ya soma juyawa kamar wacce tayi maye! hankalinta ne ya fara barin jikinta, ƙoƙarin tashi ta soma yi Uncle Artaff yayi saurin riƙota ya zaunar da ita, cikinta ne ya soma juyawa nan take ta ƙwanta aƙasin carpet tana shure-shure tareda ƙwalla uban ihu, launin kalarta duk ya sauya zuwa yellow tarr, ga wani irin ihun da takeyi tana birgima a tsakiyan falon, Mommy ganin yanda Ayush ta koma yasa ta ƙanƙame Abbah tsabar tsoro, shi kuwa Junaid hankalinsa ba ƙaramin tashi yayi ganin Ayush a cikin wannan halin, har ya motsa zai zo yanda take Uncle Artaff yayi saurin dakatar dashi ta hanyar ɗaga masa hannu kuma idonsa a rufe, jin ihun da ake yi ne yasa su Hafzat da Judan suka yo falon da saurin su, ganin Ayush ta koma yellow yasa Hafzat rungumar judan jikinta na kakkarwa, a hankali Uncle Artaff yazo ya ɗage mata rigarta sama yana tofa mata addu'o'i cikin ƙanƙanin lokaci saiga wani ɗan ƙaramin maciji ya fito ta cikin cibiyarta, a lokacin ne Ayush ta dakatar da yin shure-shure ta rufe idonta gaba ɗaya ko motsi bata ƙara yi ba, Ganin haka yasa mommy tsorita sosai kawai addu'a take ta faman zubawa, Junaid gaba ɗaya jikinsa ne yahau ɓari ganin wannan masifar, Duk waran babu wanda bai firgita ba, suna cikin wannan halin saiga wani irin baƙin hayaƙi ya bayyano wani gabjejen mutum ne ya tsaya a cikin hayaƙin, tsayinsa ya kere fankar falon gashi baƙi ƙirin dashi sai ƙaho guda biyu akansa kamar rago, idanuwansa jajawur yana sanye da baƙar riga har ƙasi, Mommy ganin wannan Aljanin yasa ta sumewa akan Sarki Raamud, itama Hafzat suma tayi ganin abunda yafi ƙarfin ƙwaƙwalwarta, Judan bai san lokacin da ya riƙota ba sauran kaɗan ta faɗi ƙasi dake a tsaye suke, Aunty Zainab matar malam ma suma tayi akan kujera Allah yaso yaran basa nan da ƙwaƙwalwarsu ce zata zauce, Judan rungumar Hafzat yayi ya ɓuya a bayan kujeru da ita, Shima Junaid da gudu yazo gefen Uncle Artaff ya tsaya kayuwansu a sama suna kallon baƙin Aljani, Cikin dirarren murya baƙin Aljani yace "meyasa ka ƙirawo ni ARTAFF?..." Uncle Artaff yace "na ƙira ka ne saboda ka cire hannunka akan wannan yarinyar ɗiyar sarki Raamud..." wani irin Dariya baƙin Aljani yayi sannan ya haɗe rai yace "indai akan wannan ne kayi kuskuren ƙira na domin sarki Raamud shi da kanshi ya sadaukar mana da ita..." Sarki Raamud a tsorace yace "Ni kuma? yaushe mukayi haka dakai?.." Baƙin Aljani yace "RAAMUD bayan kaje mana da buƙatun mu baka ko wani irin tsafi shin ya mukayi dakai? munce muna buƙatar jinin yaronka, kace bakada matar Aure balle yaro anan ka sanar mana cewa saidai jinin yaron ɗan ɗan-uwanka! Nace maka jinin yaron zamuyi amfani waran tayar da damisan ku!!! ta hanyar Damisa kuma zaka samu ko wani irin tsafi, mu muka sanya maka hannu akan ko wani irin tsafe-tsafe da kakeyi, amma da sharaɗin duk lokacin da ka karya mana tsafin da muka baka to kuwa zamu bibiyi ɗaya daga cikin ahalinka ko ɗanka ko ɗiyarka amma baza muyi amfani da yaron daka kawo mana jininsa ba saboda shi ya gama mana amfani, bazamu ƙara shiga rayuwarsa ba saidai mu shafi wani daga cikin jininka kuma ta hanyar nan zan gama da ahalinka gaba ɗaya, Bayan tsafinka ya karye mun bibiyi ɗiyarka wato jininka ba tareda saninka ba, kayi nasarar toshe kafar da zamu turo mata Aljanu amma saidai mun ajiye mata macijin huda a cikinta bayan ta cire zoben dish daga cibiyarta, daga lokacin ta zamo namu kuma muka tusa mata rashin imani a lokacin da muke so tayi mana wani aiki, mu mukayi control ɗinta ta sanya gobara agidan da take ta hanyar amfani da maciji tinda shi ba Aljani bane, saidai munyi rashin nasara matar da muke so ta mutu an ceceta, Kuma bazamu taɓa barinka kayi Aure ba shiyasa muke control ɗiyarka akan karta bari ayi Auren, kuma matarka mu muka sanyata ta mutu ta hanyar Munafurr, munyi rashin nasara akan Junaiduu, wannan macijin da muka sanyawa ɗiyarka da zaran ta haihu zamu sheƙeta sannan mu ɗauke Jaririn, kuma munyi alkawarin kaima sai mun janye jinin jikinka...." wani irin haɗiyar yawu sarki Raamud yayi duk ya haɗa gumi, Artaff yace "Baƙin Aljani muna neman Alfarma daka bar alhalin nan tinda basuyi maka komai ba, sarki Raamud shine mai laifi kuma shima muna neman yafiyarka akan ka barshi haka..." Baƙin Aljani yace "Artaff duk da nasan kaima acikin ahalin kake amma banyi garajen shiga rayuwarka ba sakamakon kayi karatu ne agurin babban malamin Aljanu kuma muna matuƙar jin maganarsa don haka kaima zamu saurari maganarka albarkacin babban malami..." Artaff yace "Nagode Baƙin Aljani amma ka barshi yayi Aurensa sannan yarinyar nan ka barta haka, tanada zuciyar imani kar ka sanyata ta zamo munguwa, Ata sanadiyarka ta zauna agidan kurkuku kuma karka taɓa mata yaran da zata haifa, na roƙeƙa idan har nima zakaji maganata to kabar mun Ahalina..." Baƙin Aljani yace "shikenam! Shikenam zamu tafi mubar maka ahalinka amma kada a sake neman mu..." Artaff yace "babu wanda zai sake hulɗa daku acikin Ahalina nayi maka alƙawari..." Ayush tana kwance bata san awani duniya take ba Baƙin Aljani ya ɗagota sama da hannu ɗaya sannan ya ɓace da ita ɓatt!!! Junaid a zabure yayo gurin da Baƙin Aljani ya tsaya sai ƙwalla ƙiran Ayush yake yana faɗin "Ina Yushert take, ina ya kaimun ita, Yushertttt! Yushertttt!! Yushertttt!!! ya tafi mun da ita, Uncle! Uncle!! kayi wani abu dan Allah kasa ya dawo mun da ita please 🙏 please 🙏...." Uncle Artaff yazo gurin da Junaid yake ta surutai kamar wani taɓaɓɓe ya dafa kafaɗarsa yace "ka kwantar da hankalinka Junaid bawai ya tafi da ita bane, kaje ɗakinku zaka sameta cikin ƙoshin lafiya..." Junaid yana jin haka ya ruga da gudun gaske ya haura Upstairs, yana zuwa yasa hannu da ƙarfi ya bankaɗa ƙofar kwatsam saiya tarar da Ayush kwance akan katafaren gadonsu sai sharar bacci take ga kuma cikinta shima yana nan lafiya, da sauri ya ƙarasa wajen gadon ya ɗale tareda rungumota jikinsa da ƙarfi kamar wanda za'a ɗauketa, yayi shuru yana rungume da ita .... Shi kuwa Uncle Artaff masifa ya shiga yiwa Abbah yana faɗin "gashi yanzu duk saboda kai waɗannan bala'in suke faruwa akan ƴaƴanku, saboda abun duniya ka sadaukar da rayuwar ƴaƴanka haba wannan wani irin rayuwa ne, abu yaƙi ƙarewa tin shekarun baya, daga wannan masifa sai wannan, Aljanu ne suke ta bibiyan rayuwar ahalin mu duk saboda kai, gashi ka jefa rayuwar ɗiyarka cikin masifa badan anyi gaggawar dakatarwa ba, yanzu inda ban ankara ba sai ta haihu su kasheta kuma a rasa dalilin mutuwar ta sannan su ɗauke jaririn, ina fatan Allah ya kawo mana ƙarshen wannan abun daga yau, Auren da kakeso kayi da bazasu taɓa barinka kayi ba kuma kuzo kuna ganin laifin yarinya alhalin ba ita take control kanta ba..." Sarki Raamud tagumi yayi yana zubda hawaye kamar wani ƙaramin yaro, Uncle Artaff ne ya nufi frig yaje ya ɗauko ruwan sanyi yazo kan mommy ya yayyafa mata a firgice ta farfaɗo tana addu'a, yazo kan matarsa itama ya yayyafa mata, har zai zauna ya hango ƙafar mutum ta bayan kujera zuwa yayi ya leƙa yaga Judan a zaune yana rungume da Hafzat wanda shima alamun a sume yake, suma haka yabi duk ya wawwatsa musu ruwan, a firgice suka farka suna jan numfashi, zuwa yayi ya zauna yana binsu da kallo, mommy ce tayi magana tareda faɗin. "wai meyake faruwa ne? wallahi bansan ya akayi ba muna cikin magana bacci ya ɗauke ni..." Aunty Zainab itama magana tayi tana bubbuga goshinta tace "nidai kafin na fito nasha maganin mura ne, ina tunanin shine yayi mun aiki yanzu..." Hafzat ganinta a jikin Judan yasa tayi saurin tashi tsaye a zabure tana faɗin "meye haka kuma, me kamun? na shiga uku yau nine ajikin ƙaton gardiii..." ta fashe da kuka tareda nufan ɗakinta da gudu cikin jin kunyar kanta. Shima kansa bai san taya hakan ya faru ba, mamakin kansa ya shiga yi, jiki a sanyaye ya miƙe tsaye yana tangal-tangal kamar mai shaye-shaye haka ya nufi ɗakinsa, Uncle Artaff ne ya miƙe tsaye tareda cewa ku jirani ina zuwa! haka ya haura upstairs ya nufi ɗakin su Junaid, yana zuwa ya tarar da ɗakin a buɗe ko tsaya rufewa Junaid baiyi ba, Uncle Artaff ne ya shiga ɗakin da sallama a bakinsa, tarar da Junaid yayi yana ƙwance ya rungumi Ayush a jikinsa, yaje har inda gadonsu yake yace "Junaid insha Allahu daga yanzu bazaku ƙara samun wata matsala akan Ayshert ba, abubuwan da tayi a baya ba yin kanta bane kuyi haƙuri, yanzu dai zamu tafi gida gobe kazo gidana zamu tattauna akan maganar Auren Mamanka da kuma sarki Raamud, kuma nasan yanzu Ayshert bazata farfaɗo yanzu ba sai zuwa cikin dare, idan kuma ta farfaɗo zata tashi da ciwon cibiya saboda wannan macijin tanan ya fito, ga wannan ka ɗiga mata a cikin cibiyar da zarar ta farfaɗo...." ya ajiye wani ɗan ƙaramin ƙwalba kamar na miski akan drawer sannan ya fice daga ɗakin, Junaid duk ya saurari abunda yace haka suka cigaba da ƙwanciyar yana rungume da ita... Shi kuwa Uncle Artaff sallama yayi dasu Mommy akan zasu tafi, Mommy tace "ku tsaya mana ku ci abinci yanzu zan girka, suka ƙi zama haka suka tafi, Su Mommy duk abubuwan da suka faru sun mance an goge musu shi acikin kwakwalwarsu kuma ba kowa bane face Baƙin Aljani domin ba kowa bane yake kallonsa balle su bada labarin suffarsa... Sarki Raamud shima jiki ba ƙwari haka ya nufi part ɗin sa, mommy ta ɗauka akan zazzaɓinsa ne ya dawo masa....... 𝑡𝑦𝑝𝑖𝑛𝑔✍️ 𝗠𝗔𝗧𝗔𝗥 𝗗𝗔𝗠𝗨𝗦𝗔 the wife of a tiger🐅🐅🐅🐅 𝙼𝚊𝚕𝚕𝚊𝚔𝚒𝚗 𝙰𝚜𝚖𝚎𝚎𝚝𝚊𝚑 ✍️✍️ 𝙿𝚊𝚒𝚍 𝚋𝚘𝚘𝚔 𝚌𝚊𝚕𝚕 𝚘𝚛 𝚠𝚑𝚊𝚝𝚜𝙰𝚙𝚙 09065443871 *💫💫{{N W A}}💫💫* Book two C̶h̶a̶p̶t̶e̶r̶ 76 to 80 Misalin ƙarfe 2Am cikin dare Junaid yana rungume da Ayush ɗinsa ko bacci bai samu damar yi ba, yaji Ayush sai mutsil-mutsil take tayi sai a lokacin ta farfaɗo, ba abunda take faɗin sai "Dan Allah ku ƙyale ni, ku maida Ni gida! shin ina zaku kaini wayyo mommy..." a ruɗe Junaid ya ɗagota tareda shashshafa fuskarta yana cewa "kinga Yushert ki kwantar da hankalinki babu inda zaki je, buɗe idonki Yaya Junaid ɗinki ne a gabanki..." A hankali take kokarin bude eyes dinta ganin Junaid yasa tayi murmushi tareda fadin "kenam mafarki nayi?.." Jinjina mata kai yayi tareda kai mata sumbata akan goshi, yace "are you okay?..." 'Daga masa kai tayi alamar babu komai, ta d'ago zata tashi zaune ta saki wani irin 'kara tare da kama saitin cikinta sai faman shushshutu take, Ri'keta yayi yana fadin "sorry my dear kiyi a hankali.." tace "cikina ciwo, inaso naje toilet ne". yace " ok let me carry you..." yasa hannu ya d'agota kamar wanda ya d'auki jaririya ya nufi toilet da ita, yana shigar da ita ta sau'ka tareda cewa "toh jeka waje ka jirani.." d'an turo baki yayi yana binta da kallo yace "ok don't worry maman Baby..." murmushi tayi tasa hannu tana kare fuskarta cikin jin kunya... shi kuwa ficewa yayi tareda rufe mata ƙofa, kai kawo ya fara yi a Cikin ɗakin yana jiran fitowar ta, ƙwatsam kunnuwansa suka jiyo masa sautin ihunta daga cikin toilet, Da gudun gaske ya tura ƙofar cikin zafin nama a rikice ya shiga ya sameta a tsaye sai ihu take tayi, rungumar ta yayi yana faɗin "kinga Yushert kiyi shuru ki sanar mun meya faru?..." ita kuwa babu bakin magana sai nuna masa cikin toilet take da yatsa.. ido ya zaro yana kallon wajen, cike da mamaki yace "fitsarin jini kuma?.." ƙara rungumeta yayi tareda ƙwantar da kanta saman kafaɗarsa yana rarrashinta, murya ciki yace "muje bedroom.." suna takawa a hankali har suka fita! jikin Ayush ne yake kakkarwa kamar wacce aka zuba mata ruwan ƙanƙara, zaunar da ita yayi a bakin gado sannan ya lalumi wayarsa yayi dialing call number Uncle Artaff, cikin ƙanƙanin lokaci ya ɗauka a ruɗe ya soma faɗin "Hello Uncle akwai matsala fah! Fitsarin jini take.." Daga ɓangaren Uncle kuma cewa yayi "haba Junaid ka kwantar da hankalinka mana, sai kace ba namiji ba duk wannan ba matsala bane, in tayi kwana uku tana yi shikenam, amma ka shafa mata wannan ruwan ƙwalbar dana baka.." Junaid ya amsa da "toh shikenam Uncle" Uncle yace "miƙawa Ayshert wayan..". Junaid kara mata wayar yayi a kunne tareda faɗin "kiyi magana Uncle ne.." Cikin fargaba da tsoro ta karɓi wayar tareda ƙara fashewa da sabon kuka, daƙer Uncle ya samu ya shawo kanta yana rarrashinta, shuru tayi tana sauraron duk maganar daya gaya mata sai yanzu hankalinta ya kwanta jin Uncle yace daman idan mace ta kusan haihuwa haka take fitsarin jini, daga baya suka katse wayar, ta kalli Junaid tana sauƙe ajiyar zuciya tace "har naji daɗi a raina, amma na tsorata sosai..." Murmushi Junaid yayi tareda shafar gefen fuskarta shi dai yasa Uncle ya gaya mata hakane saboda hankalinta yafi kwanciya, tashi yayi ya nufi toilet yaje ya wanke sannan ya haɗa mata ruwan zafi yanda zatayi wanka, dawowa cikin bedroom yayi sannan yasa hannu ya ɗauketa tareda nufan cikin toilet da ita yaje ya mata wanka tass ya fito da ita tana ɗaure da White towel, ya zaunar da ita akan kujerar gaban mirror yace "toh kiyi mun kwalliya mai kyau kafin na fito daga wanka nima..." ya sumbace ta akan lips ɗinta sannan shima ya wuce cikin toilet ... Kafin ya fito kuwa har tayi kwalliya kundai san kalar kwalliyar Ayush daga powder ne sai lips cream, shikenam sai turaruka data feffesa da gyaran gashin kanta tayi rolling dashi, sannan taje ta buɗe wardrobe ta ciro doguwar riga marar nauyi mai hannun breziya ta zura daga nan ta haura saman katafaren gadonsu tana jiran fitowar Oganta, Can shima ya fito ɗaure da towel cikin rashin sa'a ya tarar da ita har tayi bacci, kallonta yayi sannan yayi murmushi cikin so da ƙaunarta, shima ya shirya tsab kafin ya hau gadon saida ya shafa mata wannan maganin akan cibiyarta kafin ya kashe musu White light zuwa dark green lamp, ya ja musu mayafi... ★★★★★★ *TWO WEEKS AGO* Sauran sati biyu ƙarshen month tafiyar Junaid da Judan ƙasar california, Komai yana kan tafiya daidai, Judan da Hafzat ƙullalliyar alaƙa ne ya shiga tsakaninsu, yanzu koda yaushe suna tare hatta kitchen ma tare suke shiga suyi girki, mommy data fahimci haka tabar musu girkin gaba ɗaya, Judan baya so yayi nisa da Hafzat inba sallah ba, sai kuma wajen kwanciya shima dole ne tasa suke rabuwa, sai idan zata tafi school.. Itama mommy An yanke ranar da za'a ɗaura musu Aure ita da sarki Raamud, ranar Jumma'at mai zuwa, sarki Raamud baiso akawo wannan lokacin ba'a ɗaura Aure ba, mommy ce ta dage akan cewa sai Ayush ta haihu tukun tayi Aure, yanzu kuma an tabbatar da cewa a cikin wannan satin Ayush zata haihu, Duk wani kulawa Ayush tana samu daga ɓangaren mommy da shi kansa Junaid har Abba, tana jin daɗin kasancewa tare dasu, duk abunda take buƙata indai ata ɓangaren abinci ne toh shi ake mata... Around 12 0'clock na dare Ayush tana zaune akan sallaya bayan ta idar da sallar dare tana jan carbi, shi kuma Ogah Junaid yayi shame-shame akan gado sai shan baccinsa yake, bai ma san Ayush ta tashi ba har tayi sallah daman kullum saita tashi cikin dare tayi sallah, tana zaune kwatsam sai taji cikinta yanata juyawa da ƙarfin gaske, wani irin ƙara tayi game da kama cikin tana hura iskar bakinta a wahalce, wani ruwa taji yana ƙoƙarin zubo mata kamar meyin fitsari dasauri ta janye sallayar da take kai ta wurga gefe, nan danan rigarta ta ɓaci da jini, ga paya ta fashe wani irin murɗa take ji ga raɗaɗin ciwon ciki, gaba ɗaya ta fara fita hayyacinta, daƙer ta rarrafo bakin gado tasa hannu tana bubbugan Junaid dake ta shan baccinsa, shuru ko motsawa beyi ba, haka take kuka tana ta faman jijjigansa saidai yeyi juyi ya sake komawa bacci, ƙiran sunansa take a wahalce tana faɗin "Yaya Junaid ka tashi mana, cikina ciwo wayyo Allah, Yaya Junaid zan mutu ka tashi dan Allah, ka temaka mun cikinaaa..." Junaid kuwa baima san tana yi ba, wani irin nannauyar bacci ne ya ɗauke shi, Kuka take tana shure-shure, bata san lokacin data ƙwanta tana birgima ba, haka ta sake tashi daƙer ta kamo hannunsa tana jansa amma saidai ya tureta sannan ya juya ya cigaba da baccinsa, ga duk ta ɓaci da jini! Ganin bashi da niyar tashi yasa ta kama gadon daƙer ta tashi taje saitin kayinsa ta kafa bakinta akan kunnensa da ƙarfi ta garzaya masa cizo, A firgice ya juyo a rashin sani ya zabga mata mari har saida ta faɗi ƙasi yana kame da kunnensa ya juya ya cigaba da baccinsa, shi a tunaninsa duk mafarki yake yi, a cikin mafarkin yake jin shessheƙar kuka amma ya kasa farkawa, saima jan pillow da yayi ya runguma a madadin Ayush, ya ɗauka ita ya runguma, Ayush tana kuka ta soma rarrafe ta nufi hanyar fita daga ɗakin, ta kasa miƙe wa tsaye sakamakon cikinta da mararta sun riƙe babu halin tashi ita kaɗai, haka ta rarrafa daƙer ta buɗe ƙofar ta fice, A zaune take jan mazauninta tana sauƙa daga kan beni duk yanda taja sai wajen ya ɓaci da jini, da haka tayi nasarar sauƙa daga beni na uku, saida ta huta tukun ta cigaba daja tana ƙoƙarin sauƙa a beni na biyu, in cikinta ya juya saita ɗanyi ƙara ta jinkirta kafin ta cigaba da ja da gindi, tana kaiwa ƙarshen beni na biyun ta ƙwata a wajen saida ta gama juye-juyenta bayan ya ɗan lufa kuma du ta soma ƙoƙarin sauƙa daga beni na ɗaya shine na ƙarshe wanda zai sadata da babban falo, daƙer tana kuka da muzurai ta ƙarasa sauƙa falon tana ja a zaune, saida tazo tsakiyar falo zata nufi ɗakin mommy cikinta yayi wani irin juyi da ƙarfin gaske, taji wani abu kamar dutsi ya sauƙa mata ƙasin marar ta kamar zai fito ta farjinta a gigice ta saki wani irin ihuu sai a dodon kunnen mommy tayi sujjada kenam, ƙirjin mommy ne yayi wani irin bugawa a rikice take karanto addu'o'i acikin sujjadar amma ta kasa ɗagowa, Hafzat itama idar da sallar ta kenam don ko addu'a bata fara yi ba taji wannan ihun, a ruɗe ta miƙe tsaye tareda addu'a, kafin ta motsa ta ƙara jin wani ihun ana ƙwalla ƙiran sunan mommy, a tsorace Hafzat tace "Innalillahi kamar Aunty Ayusher..." tayi hanyar fita da gudu, kai tsaye cikin falo ta nufa tana zuwa ta tarar da Ayush ƙwance ta naɗe sawayenta jin abu yana shirin faɗowa, kuka take tana faɗin "wayyo Allah nah kayan cikina zasu zubo, kuzo ku temake niiii, mommy kayan cikina zasu zubooo..." Hafzat itama ta tsorita sosai haka ta rinƙa zarya acikin falon ta kasa aiwatar da komai sai yarfe hannayenta take tareda faɗin "wayyo Allah mun shiga uku Aunty Ayusher ɗinmu zata mutu, wayyo Allah jini ta ko ina Aunty Ayusher zuba yake, dan Allah kar ki mutu..." sai kuka itama take tayi kuma ta kasa taɓa Ayushert, suna cikin wannan halin saiga Mommy ta tafo da gudu kamar zata kife haka ta nufi gurin Ayush ta ɗagota tareda faɗin "Kiyi haƙuri haihuwa ne, ki ware sawayenki..." Cikin kuka Ayush tace "wallahi bazan ware sawayena ba kayan cikin zubowa zasu yi, kuma mutuwa zanyiii..." Mommy tace "ki ƙwantar da hankalinki yanzu hospital zamu kai ki, Ayush taya zan ɗagoki bayan kin tuƙwiƙwiye kamar maijin sanyi ki sake jikinki mu samu damar ɗagoki..." "wallahi mommy kayan ciki nane zasu zubo idan na sake jikinaa..." Mommy ganin Ayush zata iya kashe jaririn indai ba'ayi saurin kaita hospital ba yasa ta cewa Hafzat "riƙe mun hannayenta Ni kuma saina kama ƙafafuwanta mu ɗagata.." Hafzat jiki na kakkarwa tace "wallahi mommy bazan iya ba tsoro nake ji..." A fusace mommy ta daka mata tsawa tareda cewa "ki kama mun hannayenta mu fita da ita waran motar shine aiki?..." fashewa Hafzat tayi da kuka ta kasa motsawa, itama Ayush kuka take sosai tana faɗin "wayyo Allah kayan cikina zasu zazzaɓoo ku temake niiii..." Gaba ɗaya mommy ta rasa yanda zatayi ga Ayush taƙi sake jikinta balle ta ɗagota su fita, ga kuma jini yaƙi tsayuwa.. suna cikin wannan halin saiga Judan ya fito dasauri jin kururuwa yayi yawa yana sanye da baƙar jallabiya ya ƙaraso gurinsu yana faɗin "lafiya kuwa meyake faruwa ne..." Mommy a gigice ta riƙo hannunsa tana daɗin "haihuwa ne munaso mu kaita hospital ne, temaka ka ɗauketa mu tafi dan Allah..." Hannu Judan yasa ya ɗauketa tana ƙara tuƙwiƙwiye kanta saboda kar kayan cikinta su zubo.. da haka aka fita da ita har wajen parking, nan danan Judan ya tada motar suka miƙi hanyar gate, Ayush tana bayan motar kanta yana kan cinyar mommy, ita kuma Hafzat tana gaban motar suna isa wajen gate security ya yi saurin buɗe musu suka fita da gudun gaske sai hospital.... Shi kuwa Junaid yana nan rungume da pillow bai san wainar da ake tuyawa ba, sai ana ƙiran Asuba nan ma saida ya kusan makara ana shirin shiga sallah ya yi saurin tashi yana miƙa tareda jero addu'o'i, idonsa a lumshe ya zuro zara-zaran sawayensa ƙasi yana shirin tashi, kai tsaye toilet ya miƙa ya ɗauro Alwala sannan ya fito tsabar bacci yana cin idonsa bai lura da Ayush bata nan ba haka ya ɗauki jallabiyarsa ya zura yayi hanyar fita tareda faɗin "My Yushert shine yau ɗin kikayi sallarki baki tasheni ba koh?..." Daiden lokacin da ya buɗe ƙofa ya fice bai saurari ko za'a bashi amsa ba, yana sauri kar a shiga sallah ya rasa jam'i, dake kullum Ayush ce take tashin shi sallar Asuba, ana ƙiran farko zata tashe shi, Duk bai lura da jinin dake ɗakin ba amma ba lallai ya gane cewa akwai jini ba saboda carpet ne irin mai dark ɗin nan da kuma gashi-gashi a jiki, Amma Benin kam duk tiles ne indai ya kalli ƙasi dole zai gani... Shima Abban duk kururuwan da akaita yi acikin daren baiji ba dake part ɗinsa da ɗan rata kuma a lokacin ba wai bacci yake yi ba shima yana sallar daren, A harabar gidan Abban ya haɗu da Junaid sai faman sauri yake zai fita a tare suka tafi masallaci... ★★★★★★★★ A lokacin da aka kai Ayush labour room ihu take tana ƙiran sunan Yaya Junaid, a lokacin yaron ya jikkata sakamakon maƙurashi da tayi har ya daina motsi, saida aka mata wani Allura wanda zaisa yaron motsawa, Itama mommy rigar likitancinta ta sanya ta shige ɗakin, Judan da Hafzat kuwa a waje aka barsu suna zazzaune, Ana ƙiran Asuba daƙer Ayush ta haifo santalelen yaronta, ƙato dashi fari tasss kamar balarabe, tana haifansa kuwa ta suma, mommy farin ciki kamar bazata mutu ba, ganin Ayush bata motsi yasa suka ɗauko Allurar kashe jiki zasu yi mata Operation sakamakon akwai wani yaron a ciki, kuma a halin yanzu bazata iya amfana ba, hakan akayi saida aka ciro mata jarirai biyu bayan wanda ta haifa kafin, An samu ƴan uku Namiji ɗaya shine wanda ta haifa da kanta, sai kuma mata biyu bayan an mata Operation, Amma ba ƙaramin wahala Ayush tasha ba, bata cikin hayyacinta kwata-kwata, haka aka shiga gyara yaran gwanin sha'awa gasu triplets rass... ★★★★★ Bayan su Junaid sun koma gani yayi babu Ayush, saida ya ƙarashi dubata bai ganta ba tukun ya lura da jinin data ɓata, gabansa ne yayi wani irin bugawa a tsorace ya ƙwalla ƙiran ta "Yushertttt!!!! da gudu ya sauƙa down stairs ya nufi ɗakin mommy, itama ya tarar bata nan, ya fito falo nan ma yaga jini duk ya ɓata carpet ɗin, a ruɗe ya wuce part ɗin Abba, nan ya sanar masa halinda ake ciki, nan danan Abba ya shiga ƙiran wayan mommy amma saidai wayar ta barshi a gida, Abba yace "ina tunanin fah suna hospital ko haihuwa Ayush zatayi .." Junaid kamar ya nitse ƙasi haka yake jin kansa na rashin ganin Ayush kuma ga jini ta ko ina, a gigice yace "Abba muje hospital ɗin banaso na rasa Yushert..." Suma haka suka nufi hospital, Kafin ka ƙirga mintuna har sun isa hospital dake Junaid shi yake driving gudu yake bana wasa ba.. suna sauƙa ya rufa cikin facility ɗin hospital da gudu, yana zuwa ya tarar da Judan da Hafzat zaune babu wanda yayi magana acikin su, Hafzat sai faman kuka take ta gagara yin shuru, ganin halinda ya tarar dasu yasa gabansa ya ƙara yankewa gaba ɗaya ya gama tsorita, a gigice ya dafa kafaɗar Judan yana faɗin "Ina Yushert? Meya faru da ita?..." Judan yace "tana cikin can ɗakin..." Da gudu Junaid zai nufi ɗakin Judan yayi saurin riƙo shi yana faɗin "Ah ahhh ka kwantar da hankalinka Ogah, can ɗin labour room ne haihuwa ne ya tashi mata..." wani irin haɗiyar yawu yayi tareda faɗin "Allah yasa dai karta mutu..." Judan yace "insha Allah zata haihu cikin ƙoshi lafiya .." Shima Abban ƙarasowa wajen yayi dasauri yana addu'a Allah ya sauƙeta lafiya, Suna cikin wannan halin saiga wata Nurse ta fito daga cikin ɗakin tana sauri zata ɗauko abu, Junaid yayi saurin tareda yana faɗin "Ina Yushert ɗina?..." Nurse murmushi tayi tace "ta haihu..." Junaid yace "toh Amma ita fah??..". bata samu damar bashi amsa ba ta wuce saboda saurin da take yi, Can bayan wasu mintuna saiga Mommy ta fito tana kuka, Ganin tana kuka yasa duk suka tsorata, gaba ɗayansu nufo gurinta sukayi suna tambayanta Ayush, Mommy taƙi yin magana sai hawaye, Junaid cikin firgici da tashin hankali ya mannu da jikin gini, jikinsa gaba ɗaya ya mutu idanuwansa sun kaɗa sunyi jawur yana shirin zubda ƙwallah yaji mommy ta tintsire da dariya, lokaci guda ta fara tsalle tana faɗin "Alhamdulillah! Alhamdulillah!! Alhamdulillah!!! Alhamdulillah Masha Allah!!!! Allah mun gode makaaa..." taje gaban Junaid tana murna tace "wannan kukan farin ciki nake yi Ayush ɗita ta Haifi triplets ƴan uku kuma tana cikin ƙoshin lafiya...." Zaro ido Junaid yayi cike da mamaki yace "Mommmm are sure? Triplets fahh?..." Mommy tace "yesss my son..." Tsabar farin ciki Junaid baisan lokacin da ya rungumi mommy ba ya ɗagata sama yana juyi da ita..." Momy buɗe baki tayi tana faɗin "kai kai kaiiii sauƙe ni dallah ni ɗin dai ba ƴar tsana bace, kaji mun wawan yaro..." ta ƙarasa maganar tana dariya, sauƙeta yayi ya nufi cikin ɗakin da gudu, daman an rigada an shirya ɗakin da yaran gaba ɗaya anyi musu wanka an sanya musu kayan sanyi na jarirai daman an tanadar dasu, ita kuma Ayush tana kwance an gyara ta itama tana rufe da mayafi zuwa ƙirjinta har yanzu bata farfaɗo ba, ganan ledar jinin da aka ɗaura mata yana ɗiga a hankali saboda ta zubda jini sosai kafin azo asibitin ma.... Junaid yana shiga gurin Ayush ya fara nufa ya zauna a bakin gado yana shafar kyakykyawar fuskarta, ido a lumshe sai yaga ta ƙara masa kyau sosai ta ƙara fari daman gatanan kamar tsohuwar Aljana tsabar farin fata da kyau, yanzu kuma saita ƙara farin akan na baya, Daga baya suma su Abba da mommy da Hafzat da Judan suma suka shugo fuskarsu a washe kowa bakinsa a buɗe an kasa rufe shi, zama sukayi akan kujerun ɗakin kowa yana ɗaukin a bashi jariri, Mommy ta ɗauki jaririn namiji ta miƙawa Abba, ta ɗauƙi ɗayan mace ta miƙawa Judan ɗayar kuma ta bawa Hafzat, Shi kuma Junaid yana ta Yushert ɗinsa bai tsaya duba Jariran ba, Kowa a cikinsu saida ya tottofawa jariran Addu'o'in neman tsari, kafin shima Junaid ya karɓesu ɗaya bayan ɗaya yana musu ƙiran sallah a cikin kunnensu tareda Addu'o'i.... A wannan ranar farin ciki saida mommy ta ƙira ƴan uwa da abokan arziƙi duk ta sassanar musu, Uncle Artaff kam shine first ɗin ƙira, Kafin azozzo duba Ayush saida aka canza mata ɗaki zuwa wani katafaren ɗaki na alhurma ya gama haɗuwa kamar ɗakin ba'a cikin hospital yake ba, harda plasman da frig ga A.C amma saide an kashe A.C an kunna abunda yake bada ɗumi a ɗakin saboda jarirai basu son sanyi, (Nidai na manta sunan abun dake babu a house 🤣🤣)... Ga labulaye masu tsada, carpet kuma kana takawa yana nutsewa dakai, ga wasu kujeru masu kyan tsada guda bakwai, Cikin toilet kuma akwai shawer na ruwan sanyi da zafi, akwai kuma bahon wanka, anyi sa'a zuwa wannan lokacin Ayush ta farfaɗo saidai bata jin daɗin jikinta, ba jumawa saiga su Uncle Artaff da iyalansa shima sunzo hospital, a ranar anyi baƙi kam duk abokan arziƙi ne da masoya, banda ƴan uwansu mommy dake su ba'a gari suke ba, wasu suna Kaduna wasu Kano wasu Bauchi wasu kuma ba'a cikin Nigeria suke ba akwai waɗanda suke Camaroon da London da Sudan... Mommy tanada ƴan uwa sosai, saboda Junaid ne basa zuwa don idan sukazo bakinsu baya mutuwa sun rinƙa tambayar ƴan uwan mahaifin Junaid shi kuwa yaita musu rashin mutunci har koransu yake daga gidansu, kuma yayi musu warning akan kar su sake zuwa yanda suke dalilin da yasa basa zuwa kenam, amma yanzu tinda komai yayi normal duk zasu zo amma sai ana gobe suna, kuma a ranar suna za'a ɗaura Auren mommy da sarki Raamud... ★★★★★ Ranar Suna, ranar daya kama ranar Jumma'at kenam, gidan mommy ya cika da mutane, ƴan uwan mommy su sukafi yawa dake gidan babban gida ne, akwai ɗakuna part to part, kuma an ƙara tsara gidan yayi kyau sosai, an chancanza furniture's ɗin ɗakunan, sunyi bala'in kyau sosai, Ko wani ɗaki ƴan gari ɗaya ne aciki, ɗakin ƴan Bauchi daban, ɗakin ƴan Kano daban, ɗankin ƴan Kaduna daban, ɗakin ƴan Katsina daban, ɗakin ƴan Adamawa daban, ɗakin ƴan ƙasar London daban, ɗakin ƴan ƙasar Camaroon daban, ɗakin ƴan ƙasar Sudan daban, waɗannan duk ƴan uwan mommy ne sun samu wadatattun ɗakuna!!!! Sai kuma iyayen su Hafzat suma sunzo hidimar tareda ƴan uwanta kusan su goma, daga Kano suma... Ga Mutanen ƙasar Iran wato ƴan uwan mahaifiyar Uncle Artaff suma kusan su goma sun zo aciki harda mahaifiyarsa ta fara samun sauƙi Alhamdulillah ita kam ɗakinta daban aka tanadar ita kaɗai dake bata son hayaniya, Duk ƴan uwan mommy an nuna musu cewa itace mahaifiyar Máahmud Baban Junaid kuma an nunnuna musu sarki Raamud da Uncle Artaff cewa sune ƴan uwansa kuma sun gamsu sosai har suna cewa "ai kuwa suna kama da Máahmud sakk especially sarki Raamud kamar an tsaga kara..." Sai yanzu hankulansu suka kwanta ganin ƴan uwan mahaifin Junaid, Gasu Lailah suma sunzo hidimar ita da Maimoon dasu Ammy, Daga ƙasar China Aunty Adity itama tazo jin labarin ƙaruwar da Ogah Junaid ya samu, A masallacin da aka ɗaura Auren mommy da Abbah anan aka raɗa sunan ƴan ukun Junaid da Ayushert, An sanya musu sunaaa!!! Namijin yaci sunan mahaifin Junaid wato MÁAHMUD *(AREEPH)* Ita kuma ɗaya daga cikin macen ta samu sunan Mommy wato. FATEEMA *(AMREESH)* ita kuma ɗayar Junaid yayi alƙawarin indai ya samu ɗiya mace zai yiwa jarumarsa mai suna, toh wannan alƙawarin yana nan tafe an sanya mata sunaaa.. MARYAM *(ANGEL)*..... Masha Allah kowa yayi farin cikin zuwan Areeph da Amrish da Angel, hidima kamar baza'a dena ba, acikin ƴan uwan mommy akwai waɗanda suka haɗa diner party sun kashe kuɗi sosai, An yanyanka dabbobi kamar na mai domin saniyoyi akai ta yanka wa kusan guda Ashirin ga kuma raƙuma suma sun kai Ashirin har rasa yanda zasuyi da nama sukayi, Ayush tana ɗakinta dake batada wasu ƙawaye daga Lailah ne sai Maimoon sai kuma wasu ƴan mata daga cikin ƴan uwan mommy, sai ƴan uwan uncle Artaff waɗanda basuyi Aure ba da kuma masu Aure, Sun sa Ayush a gaba wai sai anyi mata kitso, ita kuwa Ayush furr taƙi domin ita tinda aka haifeta ba'a taɓa mata kitso ba tsabar tsayin gashinta, Filawar lalle ma bata yadda anyi mata ba sai jan ƙunshin ƙafa da hannu, kowa yaga lallen Ayush sai ya yi santi, kitso kuma saida aka kai ƙarar ta gurin mommy tukun tazo ta sameta, daƙer ta yadda za'ayi mata, mai mata kitson wata ƙwararriyar mai kitso ce daga ƙasar Camaroon, tana soma taɓa gashin Ayush taji wani irin laushi kamar Audiga ga tsayi kamar na masifa har kan tudun mazauninta, ta soma yi taji bazata iya ba haka tasau mata gashin tana cewa "wallahi bazan iya da wannan gashin ba, tsayinsa yayi yawa, Ni tinda nake ban taɓa ganin mai tsarin gashi kamar Aunty Ayusher ba..." wata makitsiyar ce tazo zata mata itama haka ta haƙura tace "waii bansan ya zanyi da wannan gashin ba, saidai ayi miki rolling ɗinsa amma bazai kitsu ba..." Saida mutane biyar suka kama gashin Ayush suna sakewa bazasu iya ba, Maimoon ce ta miƙawa Lailah yaronta Rapeekh tace "bari na gwada tawa basiran..." Mutanen waran kuwa haka sukayi caaa akanta suna faɗin "muma ƙwararrun makitsa bamu iya ba sai ke wanda bayin kitso kike yiba, ku ƴan Nigeria babu abunda kuka iya..." Maimoon ta kalli wacce tayi maganar tace "ke dube Ni dakyau nayi miki kama da ƴan Nigeria? Kije ki tambaya!! Larabawa babu wanda yakaisu iya abun duniya..." Wata a ciki tace "yoo duk nan waye ɗan Nigeria ne, ko itama Aunty Ayusher ai ba ƴar nan bace, kuma itama mommy asalinta bar ƴan nan Nigeria bace, ƴar Sudan ce suka zo nan Nigeria da sauran ƴan uwa ..." Lailah jin kowa yana tofa albarkacin bakinsa itama tace "Hmmm mukam ƴan asalin Nigeria ne, kuma banga dame aka fimu ba..." tana ƙarasa maganar ta kawar da kanta gefe tana wasa da Rapeekh... Ita kuwa Ayush kanta a sunkuye tinda suka fara ko motsi batayi ba balle ta musu magana, suna cikin maganganu har Maimoon tayi nisa da kitsonta, kuma kitson yana mungun tsaruwa gasu ƴan ƙananu take yinsu hakan yasa bata shan wahalar kitson, Nan danan Ayush ta fara shessheƙar kuka tana dafe da kanta, Duk suka zuba mata ido wasu suna cewa "haba Aunty Ayush kukan kitso kuma?..." wasu kuma suna faɗin "dan Allah ku bar mata gashinta tana jin zafin kitson ne, kuma kinga ba'a taɓa mata kitso ba dole taji zafi ...." wasu kuma suna cewa "kaiiii amma kitson nan yana mungun tsaruwa wallahi, ga gashin baƙi ƙirin sai yake fidda zanen kitso, kawai a ƙarasa mata tinda anyi rabi ..." Bayan awa guda Maimoon ta kammala kitson kan Ayush, daƙer ta iya ƙarasawa tsabar ciwo da yatsunta suke mata, ba ƙaramin wahala tasha ba kafin ta gama kitson, Ai kuwa haka aka rinƙa ɗauka kitson kan Ayush a photo, yayi kyau sosai gasu ƴan ƙananu, zirin kitson har kan tudun mazauninta, ga an fidda style, ba ƙaramin kyau Ayush tayi ba... Triplets kuma suna can ɗakin tsofi... ★★★★★★ Ogah Junaid sam baya son mutane sosai hakan yasa yaje ya buɗe ɗaya daga cikin gidajensa ya shiga, gidane ɗan ƙwaƙwass shi ba ƙarami ba sannan shi ba babba ba, bayan ya shiga da motarsa ciki yaje ya parker a waje guda sannan ya fito yazo ya rufe gate ɗin tareda saka key, zuwa yayi ya buɗe murfin motar ta ɗayan ɓangaren nan itama Adity ta zuro zankaɗeɗen sawayenta ta fito tana sanye da jeans da t-shirt mai dogon hannu, da ƴar jakarta, ga kuma takalmi mai tsini tayi gyaran gashi ba ƙaramin kyau tayi ba, kuma yanzu ta dena yawan faɗace-faɗace tinda taji Rumana da Angel sun mutu daga nan ta shiga taitayinta, daga baya aka koreta daga aikin soja amma Junaid yasa an mayarta yanzu tana kan Aikinta, kuma itama an saka ranar Aurenta da wani cousin ɗinta shima Soja ne.. Junaid ya kawota nan gidan ne saboda acan kowa kallonta yake ana tsegumin daga ina take kuma alhalin ba ƴar uwarsu ba, kuma basuda ƴan uwa Arniya hakan ma ƴar china, da haka Adity taje ta gano Jarirai sannan suka gaisa dasu Mommy da Ayush, ƙarasa shiga cikin falon ɗakin sukayi, ta zauna akan sofa tana fuskantar plasman, shi kuma zuwa yayi ya ɗauko musu abincin da zasu ci domin basu samu damar cin abinci ba, Shi Junaid bazai iya cin abincin gidan hidima ba, ita kuma idon mutane ne suka hanata cin abincin gidan hidimar, kuma bayan haka ma bazata iya ci acikin mutane over ba...... 𝑡𝑦𝑝𝑖𝑛𝑔✍️ 𝗠𝗔𝗧𝗔𝗥 𝗗𝗔𝗠𝗨𝗦𝗔 the wife of a tiger🐅🐅🐅🐅 𝙼𝚊𝚕𝚕𝚊𝚔𝚒𝚗 𝙰𝚜𝚖𝚎𝚎𝚝𝚊𝚑 ✍️✍️ 𝙿𝚊𝚒𝚍 𝚋𝚘𝚘𝚔 𝚌𝚊𝚕𝚕 𝚘𝚛 𝚠𝚑𝚊𝚝𝚜𝙰𝚙𝚙 09065443871 *💫💫{{N W A}}💫💫* Book two C̶h̶a̶p̶t̶e̶r̶ 81 to 85 Bayan Ansha hidimar suna dana biki kowa ya watse, sai Ayush da yaranta uku da Oganta Masha Allah suna samun kulawa sosai, itama mommy tana can part ɗinsu ita da sarki Raamud anata cin Amarci... A satin nan su Junaid zasu tafi ƙasar california tare zasu tafi da Sarki Raamud shida mommy domin cigaba da rayuwarsu a cikin masarauta, jin haka ba ƙaramin tashin hankali Ayush ta shiga ba ganin duk za'a watse a barta, Ƙwance take akan gado sai faman rera kuka take ga jarirai a gefen gado sai sharar baccinsu suke gwanin burgewa, Junaid ne ya shugo da sallama a bakinsa jin ba'a amsa masa ba yasa ya ƙara maimaitawa, still ba'a amsa ba, ƙarasa shugowa yayi cike da mamakin ganin Ayush kanta a kife sai kuka take tayi, zama yayi a bakin gado ya ambaci sunanta a hankali cikin nuna damuwa yace "Yushert meya faru dake kike kuka?..." shuru bata bashi amsa ba, yasa hannu ya ɗago da ita tareda kwantar da ita saman faffaɗan ƙirjinsa yace "Yushert gaya mun mana kar kisa nima nayi kukan, please my wife..." Ɗagowa tayi da rinanan idanuwanta waɗanda tasha kuka dasu suna kallon juna lips ɗinta na kakkarwa daƙer ta iya cewa "Zaujul! zaku tafi ku barni, bana son ku tafi ku barniii..." Nan ta ƙara fashewa da kuka daƙer ya rarrasheta kanta akan ƙirjinsa yana bubbugan bayanta a hankali yace "kiyi haƙuri My Yushert tafiya ai ba mutuwa bane, kuma nikam ai ba jumawa zanyi ba zan dawo..." tace "duk da hakan ma Ni a tafi dani..." zaro dara-daran idanuwansa yayi dasauri ya katseta da cewa "Yushert ina zan kai ki da waɗannan jarirai ba ɗaya ba, ba biyu ba kedai kiyi haƙuri idan yaran sun fara girma in yaso sai in tafi dake koh..." ƙara fashewa tayi da kuka tana faɗin "mommy da Abbah zasu tafi, kaima zaka tafi toh yazanyi.." murmushi yayi yace "gaki ga Hafiza mezai same ki, kuma kafin na tafi zan sa a nemo miki wasu matan da zasu miki renon yara da wasu ayyukan gida..." saida ya tabbatar ta haƙura tukun ya daina rarrashinta ya tashi ya cigaba da shirye-shirye domin fitar asubanci zasu yi, saboda jirginsu a wannan lokacin zai tashi, itama tashi tayi tana taya shi shirya kayayyakinsa haɗe da shan soyayya... itama Hafzat tana kitchen gaba ɗaya ta rasa sukunin ta na tafiyar Judan, ta shaƙu dashi bana wasa ba, sai sharar hawaye take tayi ita kaɗai, yayin da shi kuma yana can ɗakinsa ya gama shirinsa tsab, yana kwance akan gado yayi shame-shame kansa na kallon ceilling yana tunanin tafiyar da zaiyi yabar Hafzat, baya tunanin zai iya tafiya ya barta amma saidai ya zama dole ya tafi, dan ma Ogah Junaid ne ya tsayar dashi da tin yaushe ya tafi, ga kuma soyayyar Hafzat tana shirin zamo masa matsala indai ya rasata a matsayin matar Aurensa, haka ya dinga waɗannan tunanika... A part ɗin su Mommy kuwa suma sun gama shirinsu sauran tafiya ne ya rage musu, Abbah kamar bazai mutu ba tsabar murna da farin cikin mallakar mommy a matsayin matarsa ta sunna, kuma gashi yana ɗaukin komawa masarautarsa da matarsa, Mommy kuma ba'a son ranta za'ayi wannan tafiyar da ita ba saboda tana tunanin wahalar da Ayush zata sha waran rainon triplets, twins ma ya ake ƙarewa dasu balle har triplets, saidai dake Junaid yace mata akwai waɗanda zasu na rainon yaran, anan hankalinta ya kwanta.... A ranar kuwa aka kawo wasu mata su huɗu, ɗaya zata na aikin girki da sauran Ayyukan gida, ɗaya kuma zatana gyaran ɗakuna da goge-goge da wanke-wanke da wanki kayan yara dana uwar.... sauran biyun kuma sune masu rainon yara da sauran Ayyukan gida suma, Bayan sallar asuba su Mommy ne suka fiffito da kayayyakin su, duk suka saka su a booth ɗin motar kai tsaye suka shiga falon su Ayush, zasu musu sallama Ayush tana kuka haka suka sauƙo falo ita da Junaid tana riƙe da hannunsa, kowa ya hallara a falon mommy taje gaban Ayush tana goge mata hawaye tace "kiyi haƙuri Daughter kema ba jumawa zaki iso mu, Addu'a muke buƙata daga wajenki..." Ayush tana kuka haka ta rungumi mommy tana faɗin "Allah ya kiyaye hanya mommy amma zanyi kewarku sosai..." itama mommy kuka take ji take kamar ta haƙura da tafiyar.. Daƙer suka raba jikinsu Ayush ta nufi gurin Abbah shima ta rungume shi tace "Abbbaaahhh..." anan ta ƙara fashewa da kuka, daƙer Abbah ya rarrasheta tayi shuru... Itama Hafzat kuka take na rashin ganin Mommy da Judan ɗinta, Judan sai faman rarrashinta yake amma taƙi yin shuru, saida mommy tazo itama ta rungumeta tana rarrashinta tukun ta haƙura, kafin su bar falon saida suka sanyawa triplets Addu'o'i tukun, suna fita suka tarar da Uncle Artaff shima yazo yin rakiya zuwa Airport domin shi tin jiya sukayi sallama, Junaid bai samu fitowa harabar gidan ba yana can falo shi da Ayush ya rungumeta sosai a jikinsa kamar zai mayarta cikin cikinsa shima har da ƙwallarsa domin ba ƙaramin kewar ta zaiyi ba, Bayan sun gama rungume² suka fito kowa a cikinsu jiki ba ƙwari, duk sun shiga motar shi kawai ake jira, kafin ya shiga motar saida ya rabawa Ƴan Aikin da aka kawo kuɗi kowa saida ya bata dubu ɗari bibbiyu sannan yaja musu kunne akan baya son ƙazanta da nuna rashin gaskiya, saboda haka ne yasa akaje har ƙauyen suleja aka ɗauko su domin sunfi ƴan gari riƙon Amana kuma su basu fiye zalontoma kamar ƴan cikin gari ba, itama Hafzat saida ya bata kuɗi dubu ɗari biyar yace "kuɗin kashewarta ne idan tana buƙatar wani abu, kuɗin school fees kuma idan an buƙaci hakan tayi magana za'a turo mata...". Hafzat karɓa tayi tana godiya banda kuɗin da Judan ya bata Dollars goma, ko wani guda ɗaya dubu ɗari ne idan ta canza su sun zama one million kenam, mommy da Abbah suma suka bata two millions... Ayush kuma shi kansa Junaid baisan adadin kuɗin daya ajiye mata ba, domin suna nan jaka guda a cike da kuɗi banda wanda mommy ta bata nan ma sunfi millions goma, ga Abbah yazo ya ƙara mata da Dollars domin shi baya amfani da Naira, waɗannan sun bata ne saboda idan madarar babies suka ƙare ta siya musu, sun faɗa mata hakane saboda sun san Ayush sam bata iya kashe kuɗi ba, yanzu dubu ɗari sai tayi shekara bata kashe su ba, madarar babies suna nan kamar ruwan randa, ba'a tunanin zasu ƙare a watanni kusa ba, Da haka sukayi sallama suka tafi, juyawa Ayush tayi da gudu tana rera kuka bata tsaya ako ina ba sai a cikin ɗakinta, domin tasan bada wuri Junaid zai dawo ba, su Mommy kuwa sun tafi kenam... Triplets kuma suna can waran masu rainon su, itama Hafzat ɗakinta ta shige tana kuka, Gidan kuwa an zuba masu tsaro kam ba laifi dake iya mata ne kawai aciki, Bodyguards saida aka zuba guda goma, baƙaƙe da fararen fata kowa yana riƙe da manya-manyan bindigu, suna toshe da baƙaƙen glass, sunci boom kai kace tinda aka halicce su basu taɓa yin dariya ba, Ga wasu karnuka na turawa da aka zuba suma sun kai biyar, waɗannan manya manyan karnukan Aikinsu zagaye duk faɗin gidan ne, daga sunji motsi su hau haushi, sai kuma wasu daga cikin Bodyguards su yo gurin.... Hafzat da direbanta mai kaita school, fitarta a gidan sai in za'a kaita skull idan kuma ta dawo shikenam ba sake fita sai washe gari kuma du, shiyasa duk tilin kuɗin da aka basu suna nan a ajiye basa kashewa saboda ba'a barin kowa ya fita haka kawai, kuma duk abunda zasu siya akwai shi a gidan, duk abunda suke so akwai a gida, saidai ita Hafzat dake tana da waya ta aika kuɗinta bank duk aka zube mata su acikin account duk sanda ta tashi takan turawa iyayenta kuɗi ta hanyar transfer... (Tabb nikam duk kuɗin da aka ajiye mun bazan iya zama ba yawo ba yaciin🙄🙄🙄 anya kuma zaku iya kuwa Reader's?....) Rayuwa tana tafiya yanda ya kamata, abubuwa suna chanzawa zuwa hanya mai kyau, akwana a tashi yau wata biyar da tafiyar su Mommy, kullum Ayush sai tayi waya dasu ta video call acikin computer, wani sa'in kuma a cikin ƙatuwar wayarta Iphone take waya dasu, especially Ogah Junaid kusan kwana suke suna waya ta video call, hakan yana rage mata kewa sosai, yanzu Ayush saita jera sati guda bata sauƙo falo ba, abinci saidai akai mata can upstairs, daga bacci sai kuma waya da Junaid ɗinta sai idan lokacin sallah yayi ta tashi tayi acikin ɗakinta, takan motsa jiki wajen gyara cikin ɗakinta domin bata yadda ƴan aiki su shugo mata bedroom sai iya Hafzat ce kawai ta lamince mata, itama sai idan zata zo ɗaukan yara takai su wajen raino, ba'a maiso mata dasu sai idan dare yayi, tin suna wata uku ta yayesu bata basu nono sai madara, ai kuwa yaran gwanin burgewa gasu ƴan ɓulɓul dasu duk da basa shan nono... Itama Hafzat tin da safe idan ta tafi school bata dawowa Sai ƙarfe shida na yamma dake makarantar haɗe take da Boko da islamiyya, idan ta dawo tayi wanka taci abinci sai tayi waya da Judan tukun take ƙwanciya bacci bayan nan tayi sallar mangarib... Kuma sa'in-sa'in Uncle Artaff yakan zo gidan dubasu ko akwai wacce bata da lafiya ko kuma akwai wata matsala..... ★★★ *AFTER 3 YEARS AGO* ★★★ Ogah Junaid aikinsa ya kankama a ƙasar California, yanzu aiki yake tuƙuru na aikin General, bai tashi dawowa Nigeria ba saida yayi shekara uku kafin, domin dayaje riƙeshi akayi aka hanashi dawowa, yanzu saidai ya rinƙa zuwa hutun ƙwana biyu saiya koma, Dawowarsa ba ƙaramin farin ciki Ayush ta shiga ba, harda kukan farin ciki, Ogah Junaid ya ƙara kyau sosai yayi fari duk wanda ya ganshi yasan ya samu kyakkyawar kulawa da jin daɗin rayuwa, shima ba ƙaramin farin ciki yayi ba ganin iyalansa cikin ƙoshin lafiya, ga yaransa sun girma sosai yanzu duk sun wuce shekara uku² da haihuwa, Ayush itama ta ƙara kyau sosai ta samu hutu tayi ƙiba, jiki ya murmure.... Hafzat tayi candy ta samu result mai kyau, dake yanzu school of Nursing ta kammala ta karanci Pharmacy na shekara biyu... Gaba ɗayansu suna zazzaune a falo suna kallon India Film na yaƙi Ayush tana zaune a kusa da Junaid ɗinta ga yaransu ɗaya tana can ƙwance saman cinyar Hafzat, ɗaya kuma tana kan cinyar Daddynta.. Junaid yana riƙe da little Angel akan cinyarsa yana wasa da ita tareda faɗin "Jaruma ta kenam, wannan ita ce jarumata kuma Soja ta...". ta ɗago tana kallonsa cikin Muryar yara tace "Daddy nikam Soja zan zama idan na girma ko?..." cikin so da ƙauna ya sumbaceta akan goshi yace "yawwa Jarumata shiyasa nake ƙara ƙaunarki ai, kinga takwararki ma Soja ce ta iya faɗa sosai..." tace "Daddy ai Mommy ta nuna mana photonta da kayan sojoji ajikinta tamun kyau sosai...". murmushi yayi yace "kema ai haka zaki zama, kiyi kyau acikin kayan sojoji..." Little Angel cikin zaƙewa takai hannunta saitin goshinta tana faɗin "jinjina ga tutar sojoji..." daga nan ta sara wa Daddynta.. Gaba ɗaya kwashewa sukayi da dariya, Ayush hannu tasa ta maki gadon bayanta tana dariya, kuma daman Little Angel ta fisu surutu da iyeyi, Junaid ya kalli Ayush cike da mamaki yace "duk waye ya koya mata wannan?..." Ayush ɗaga kafaɗarta tayi alamar itama bata saniba, Hafzat dake kujerar gefe dasu sosai tace "wallahi duk a Film take gani, kuma tafi kallon Film ɗin sojoji..." Junaid ƙara rungumarta yayi tareda lumshe idonsa yana hasasho fuskar Angel marigayiya, gaba ɗaya ta dabaibaye masa ƙwaƙwalwa, saida ya gama tunaninta tukun ya buɗe eyes ɗinsa a hankali ya maida kallonsa kan Amreesh yayi mata alamar tazo ta, tana can tana kwance saman cinyar Hafzat ta taso tazo gabansa tace "gani Daddy..." Da murmushi akan fuskarsa yace "ke kuma pah idan kin girma wani aiki zakiyi?..." Ɗan turo ƙaramin lips ɗinta tayi tana haɗe gira tace "Ni nikam Aure zanyi..." Zaro ido Junaid yayi yana binta da kallo, Ayush kuwa ruwa ta kora a bakinta amma jin abunda Amrish ta faɗa yasa ta burtso da ruwan tana kwashewa da dariya harda kama cikinta, Junaid yace "Keee leave my front dalla dubeta, waii Aure kuttt..." Kallon Ayush yayi ganin sai dariya take yasa ya haɗe rai tareda faɗin "ke kika ɗorata akan keken ɓera koh?.." Ayush toshe bakinta tayi da hannu tana ƙunsar dariya tace "Ni kuma? wallahi ban taɓa musu maganar Aure ba...". yace "amma tayaya tasan ana yin Aure?.." tace "taya bazasu sani ba bayan yaran sunyi wayo yanzu fah shekara huɗu suka nufa, kuma ko a makaranta ai zasu ji ana maganar..." Yace "ƙarya kike babu yanda za'ayi ƴan Nursery school ayi musu maganar Aure, dole ma duk na tattara ku mu koma ƙasar waje saboda kar a lalata mun yara da maganar Aure..." ya ƙarasa maganar yana kallon Amrish ya kuma cewa "ke kuma ko Takwarar ki Mommy saida tayi karatu ta samu Aiki tukun tayi Aure, Babbar likita ce don haka kar na sake jin kinyi maganar Aure kinji koh?..". dasauri ta ɗaga masa kai ganin ransa a haɗe, ya kuma cewa "wai ma waye yace miki kiyi Aure?.." tayi saurin nuna Ayush da yatsa tace "Mommy ce..." zaro ido Ayush tayi tana kallonta a ruɗe tace "Ni kuma Amriish? yaushe nayi miki maganar Aure?..." Junaid wani irin kallo yake watsa mata yace "yaro ai bazai yi ƙarya ba" ta juyo da kallonta kansa tana faɗin "wallahi tallahi bani bace, taya zanyi musu maganar Aure bayan nasan har yanzu basu datu ba, du Da du yaushe aka haifesu balle nace zan sakasu a gaba nayi musu....". kafin ta kai ƙarshen maganar ta yayi saurin ɗaga mata hannu tareda cewa "ya isa haka banson long story.." Ayush hararar Amrish take da gwala-gwalan idanuwanta tana mamakin yaushe yarinyar nan ta koyi ƙarya haka... Amrish kamar zata fashe da kuka, ta nufi gurin Hafzat daman itace uwar ɗakinta, Amriish tafi kama da Ayush sosai kamar an tsaga kara, duk wata suffar ta irin na Ayush ce har tsayin gashi domin tafi little Angel sumar gashi, kuma tafi little Angel farin fata sosai duk da itama little Angel tanada haske amma bata kai Amrish haske ba, Ita little Angel yanayin fuskarta irin na Junaid ne hatta launin haskensu, dan Junaid ko rabin ɗauko farin Ayush baiyi ba, Shi kuma Areeph duk wani hali na Junaid ya ɗauko su, kwata-kwata an rasa kamannin wa ya ɗauko acikin Sarki Raamud da kuma Baban Junaid wato Máahmud takwaran Areeph.. Junaid ne ya fara waige-waige yana faɗin "Ni ina Areeph ne?...". Ayush tace "yana ɗakinsa.." Yace "ha'a toh shi baya fitowa cikin mutane ne?.." Little Angel tayi cabb ta tari bakinsa da cewa "Laaa Daddy shikam baya zama acikin mutane, daga ɗakinsa sai cikin ɗakinsa, kuma yana wasan game ɗin harbi da bindiga a cikin computer sa..." Junaid yace "kenam shima soja zai zama ...". Little Angel ta kuma cewa. "ehh mana ai we are together me and him...". Yace "wow my Jaruma Ina yinku over, jeki ƙira mun shi oyaaah..." ta sauƙa akansa da gudu ta nufi ɗakinsa, tana zuwa ta tura ƙofar ɗakin ta shiga ta tarar dashi yanata wasan game ɗinsa na sojoji da ƴan fashi, juyowa yayi yana kallonta up and down rai a haɗe yace "ke Ni abokinki ne zakina shugo mun ɗaki babu excuse?..." tace "toh Daddy ne yake ƙiranka..." yace "yi mun kneel down a wajen" turo baki tayi tace "cab ɗin wallahi bazanyi ba kai Uba nane..." Areeph tasowa yayi a fusace yana zuwa gabanta ya talleta da mari da ɗan ƙaramin hannunsa, yana faɗin "Ni ba abokinki bane...". Da gudu little Angel tabar ɗakin tana kuka hannu riƙe da fuska, tana zuwa falon tace "Daddy ya mareni..." Junaid cike da mamaki yace "ya mareki kuma?..." sai a lokacin Ayush tayi magana tana cewa "daman ai nasan hakan zata faru, shifa Areeph baya barin kowa ya shigar mar ɗaki sai iya Ni kaɗai..." suna cikin maganar sai gashi ya fito yana kuncume da fuska ko alamar dariya babu, yana zuwa ya nemi guri ya zauna, yana fuskantar Ayush yace "Mommy ke kike ƙirana?..". girgiza kai Ayush tayi tana nuna masa Junaid da yatsa baki ya gagara buɗuwa tsabar ƙunsar dariyar da take yi a cikinta saboda ganin yanda Junaid ya ƙafe idonsa akan Areeph ko ƙibtawa baya yi gaba ɗaya yaron ya bashi mamaki ganin yanda yake abu kamar babban mutum, Areeph kallon Daddynsa yayi sannan yace "gani toh, sauri nake ina uzuri...". Junaid ne ya danƙwale shi tareda faɗin "dan ƙaniyarka uzurinka yafi ƙirana muhimmanci?.." Girgiza kai Areeph yayi tareda cewa "a'ah shiyasa na bar uzurin nazo Ni ai...". jinjina kai Junaid yayi sannan yace "meyasa ka mari Angel?..". kawar da kai Areeph yayi gefe yana mutsil-mutsil da baki daƙer ya iya furta "ta raina Ni ne kuma a ƙarƙashina take...". Zaro ido Junaid yayi yace "kai kake iko da ita?..." Areeph yace "eh mana Daddy saboda duk gidan nan nine namiji, ni kuma bazan jure raini ba zan iya murɗe musu wuya..." sake baki Junaid yayi yana kallonsa, Ayush kallon Junaid tayi tana tuna yanda shima yake maganarsa a baya Abu kaɗan sai yace zai murɗe wa mutum wuya toh gashi yaronsa duk ya ɗauko irin halayensa da kuma yanayin maganarsa, Jinjina kai Junaid yayi baiga laifinsa ba saboda shima yayi ire-iren waɗannan abubuwan, daƙer ya buɗe bakinsa yace "okay it's okay, daman tambayarka zanyi idan ka girma wani irin aiki zakayi ?..." Areeph saida ya gama juye-juyensa da ɗagun kai saida yaɗau kusan mintuna tukun ya buɗe baki yace "Doctor.." ataƙaice... Junaid yace "kenam a ƙarƙashin mata zaka ƙare?..." Areeph kallon Daddynsa yayi sannan yace. "ra'ayina na faɗa zan kuma iya canzawa idan naso..." yana kaiwa nan bai tsaya sauraron abunda za'a ƙara cemasa ba ya tashi zai koma ɗakinsa, har zai haura stairs ya sake juyowa yace "nifa kar a sake shugo mun ɗaki, duk yarinyar data shugo kuma zan karyata ne...". ya maida kallonsa kan Ayush ya kuma cewa "mommy kizo ki mun wanka...". yana ƙarasa maganar ya fara ɗale stairs yankinsa daban ne, ba kowa ne yake zuwa wannan yankin ba sai Ayush kawai, ita zataje tayi masa wanka sannan takai masa abinci domin baya ci acikin mutane, idan lokacin tafiya makaranta ne haka Ayush zataje ta shirya shi ya fito su tafi makaranta, amma bayan makaranta baya fitowa daga cikin ɗakinsa, Shikam Areeph har yaso yafi Babansa girman kai da jiji dakai da kuma ɗagun kai... Junaid kamar wanda aka watsa mar ruwan sanyi haka ya ƙafe a wajen, a tsorace ya kalli Ayush yace "anya ba ƴaƴan Aljanu kika haifa mun ba? especially Areeph du Da du how many years ?? Bai fa shiga shekara huɗu ba?...". a ruɗe yake wannan maganar idonsa akan Ayush, Itama Ayush jiki a sanyaye ta tashi ta nufi ɗakin Areeph ba tareda tace komai ba, Girgiza kai yayi ya furta "impossible zan gyara shi, I'll make him a good parson..." ya kalli su Little Angel da Amrish yace "Oyaah kuje ɗakinku kuje ku kwanta ko, gobe akwai school...". tashi suka yi suka nufi ɗakinsu suma ɗakinsu yana can saman stairs... Shima miƙewa yayi zai tafi ya kalli gurin da Hafzat take yace "ke ma Yakamata kije ki kwanta koh dare yayi ƙarfe 10 yanzu?.." ta amsa masa da "toh" har ta miƙe zata tafi ɗakinta ya tsayar da ita yana cewa "Judan yamun magana yace next week zai turo iyayensa daga nan zamu wuce dasu can garinku muje mu samu iyayenki akan maganar Aurenku, tinda har kin kammala karatun ki...." Hafzat bata san lokacin data sau murmushi ba tace "toh Uncle Allah ya kaimu..." ta juya da gudu ta nufi ɗakinta, Shima Upstairs ya haura ya nufi ɗakinsu... Itama Ayush saida ta wanki Areeph ta shirya shi cikin sleeping dress ya ƙwanta akan gadonsa ta tottofa masa Addu'o'i tukun ta rufe masa ƙofa, kai tsaye ɗakin ƴan mata ta nufa suma taje ta gyaggyara musu ƙwanciya ta rufesu da mayafi sannan ta yi musu addu'o'i suma ta kulle musu ƙofa, daga nan ta nufi ɗakinsu, tana zuwa ta tara da Junaid har ya shiga wanka, itama shiryawa tayi cikin kayan bacci ta haura saman gado, ba jumawa shima ya fito ya shirya sannan ya haura shima, anan aka fara love an daɗe ba'a haɗu ba, kowa yana kewar kowa, Kashe hasken ɗakin sukayi daga nan suka shige mayafi, (Asmeetah kuma tayi ficewar ta, domin kar taga abunda zai hanata bacci🤪🤪) ★★★★★★ Alhamdulillah 🙏 An fitar da Doctor Hasheem daga prison, amma daƙer aka samu ya fito jiki duk ya jikkata, Kai tsaye gidansa aka nufa dashi aka bashi Makullin gidan ya buɗe ya shige abunsa, gani yayi gidan yayi datti over dake bamai shugowa gidan tsawon shekara huɗu, haka ya shiga yaje ya watsa ruwa a jikinsa, saida yayi wanka sau biyar, yana gamawa zai ƙara yi kuma du saida yaga jikinsa yayi fes tukun, shi da kansa yaje kitchen ya girka abunda zai ci, Gidan nan kuwa haka yasa aka turo masa masu gyara suka zo suka gyara gidan tass, Gaba ɗaya furniture's ɗin ɗakin duk yasa an canza su, komai da komai an gyara gida ya koma normal, Doctor Hasheem saida yayi wata guda acikin gidansa bai leƙa waje ba, saida ya tabbatar jikinsa yayi normal, haskensa ya bayyano duk ya hashaske gemun fuskarsa yayi gyaran fuska yayi kyau sosai, komai nashi ya dawo normal tukun ya yanke hukuncin zaije gidan su Maimoon domin saka yaronsa a idonsa, yanzu baima san ya kamannun yaron yake ba, ga kuma ƙanwarsa Lailah a gidan dole zaije ya gansu, tinda Daddyn Maimoon shida kansa yasa aka fito dashi, Ita Lailah tana yawan zuwa prison gano Yayanta... Fitowa harabar gidan yayi yana sanye da jamfa a jikinsa da hularsa duk yasa an wanke masa motocinsa saida ya zaɓi ɗaya daga ciki tukun yaja saida yaje wajen gate kuma du ya fito ya buɗe gate da kansa ya koma cikin motar ya fita, yana fita ya ƙara fitowa ya rufe gate yasa key, Kai tsaye gidansu Maimoon ya nufa... Yana zuwa ƙofar gidan yaje yayi parking da motarsa a waje guda sannan ya fito yazo yana knocking, ƙirjinsa kuwa haka yake masa bugun tara-tara, domin gidan ƙwarjini yake masa, cikin sa'a saiga gate man ya buɗe suka gaisa, daƙer maigadi ya iya gane Doctor Hasheem saboda shekaru har huɗu ba wasa bane, Cikin ikon Allah yana shiga wantalelen gidan daga nesa ya hango wani ƙaramin yaro yanata buga ball shi kaɗai sai faman gudu yake, Da haka har Doctor Hasheem ya ƙaraso wajen yaron fuska ɗauke da murmushi yace "fine boy how fi?.." yaron tsayawa yayi yana kallonsa cikin rashin sani, buɗan bakin yaron yace "waye kai?.." Doctor Hasheem rage tsayinsa yayi ya durƙusa a gaban yaron tareda dafa kafaɗarsa yace "what's your name?.." yaron yace "my name is Abubakar better known as Rapeekh...". Doctor Hasheem yace "wow Nice name, which class are you?..." Rapeekh yace "Nursery 2..." Ya kuma cewa "how old are you?..". Rapeekh yace. "I'm forth years old...". kafin Doctor Hasheem ya kuma sake masa wani tambayar Rapeekh ya katse shi da cewa "And than you, please should will tell me your own details?..." murmushi Doctor Hasheem yayi yana jinjina kai, kafin ya buɗe baki yayi magana yaji daga nesa ana cewa "Kai Rapeekh kai da waye a wajen nan?.." juyawar da zaiyi ƙwatsam yaga Maimoon ta nufo gurinsu da sauri, ganin Doctor Hasheem yasa gabanta faɗuwa da ƙarfin gaske ta furta "A"uzubillahi mina shaiɗanin rajinn, meya kawo ka gidan mu? shin waya fito dakai daga prison? Nayi tunanin acan zaka ƙare rayuwarka ai..." Dasauri Doctor Hasheem ya miƙe tsaye sam baiji daɗin kalaman Maimoon ba, Lailah da Doctor Mansur suna can wajen flowers ɗin gidan suna ta shan soyayyarsu, basu ma san Doctor Hasheem ya shugo gidan ba sai muryar Maimoon suka jiyo tanata maganganu a fusace, tasowa sukayi suka nufo wajen dan tabbatar da abunda ke faruwa, Lailah ganin Yayanta yasa tayi ihu ta tafo da gudu ta rungume shi sosai tana tsallan farin ciki, shima rungumarta yayi yana faɗin "Autar Mama nayi kewarki..." tace "nima haka Yayanaaa nayi farin cikin ganinka..." Bayan sun gama tace "Yayana yaushe ka fito daga prison?..." Yace "Auta watana guda da fitowa.." Ta ɗan turo lips ɗinta tace "Yaya shine baka nemeni ba tsawon wata guda da fitowarka..." Tace "Amma Yaya Daddy bai sanar mana cewa an fitar dakai ba...". Murmushi kawai yayi bai bada amsa ba, Doctor Mansur ne ya miƙa masa hannu yana faɗin "your welcome my friend...". suka gaisa sosai cike da kewar juna.. Suna cikin wannan halin saiga Daddy ya shugo da motarsa, parking yayi sannan ya fito yazo wajen yana gyaran murya tareda faɗin "meyake faruwa anan?..." Jikin Doctor Hasheem ne yayi sanyi ganin Daddy, Daddy ne ya kalli Doct Hasheem yace "Ohh kazo ne, naga shuru-shuru ban ganka kazo ba, shikenam tinda Allah yasa kazo ku shiga ciki inason magana daku gaba ɗayanku..." ya kalli Doctor Mansur yace "harda kai kaima..." daga nan yayi wucewarsa ciki, Maimoon riƙo hannun Rapeekh tayi taja dogon tsuka sannan tayi wucewarta itama, daga baya suma suka nufi ciki.... *TOH PAH LITTAFI YAZO ƘARSHE, SAURAN ƘIRISSSSS...* 𝑡𝑦𝑝𝑖𝑛𝑔✍️ 𝗠𝗔𝗧𝗔𝗥 𝗗𝗔𝗠𝗨𝗦𝗔 the wife of a tiger🐅🐅🐅🐅 𝙼𝚊𝚕𝚕𝚊𝚔𝚒𝚗 𝙰𝚜𝚖𝚎𝚎𝚝𝚊𝚑 ✍️✍️ 𝙿𝚊𝚒𝚍 𝚋𝚘𝚘𝚔 𝚌𝚊𝚕𝚕 𝚘𝚛 𝚠𝚑𝚊𝚝𝚜𝙰𝚙𝚙 09065443871 *💫💫{{N W A}}💫💫* Book two C̶h̶a̶p̶t̶e̶r̶ 86 to 90 Kowa ya hallaru a falo ana sauraron abunda Daddy zai ce, Ga Ammy a kusa dashi, Doctor Hasheem kuma yana zaune akujera ɗaya da Doctor Mansur, Maimoon da Lailah kuma suna zaune aƙasin carpet, Daddy yana ɗauke da Rapeekh akan cinyarsa ya fara magana kamar haka "Ba komai ne yasa duk na tara ku anan ba sai don na tabbatar muku da wani sirri, sannan na magance matsalar data daɗe da afkuwa, anyi mun abunda banji daɗinsa ba sam.." ya kalli Doctor Hasheem sannan ya kalli yanda Maimoon take ya girgiza kai tareda faɗin. "haƙiƙannin gaskiya baku yiwa kanku adalci ba, amma ba laifinku bane, duk laifi nane dana barku kara zube bayan nasan akwai ƙulalliyar alaƙa a tsakaninku..." Daddy ya ambaci sunan Dactor Hasheem murya a sanyaye yace "Hasheem kayi haƙuri abunda nayi maka, nayi hakane saboda ka gyara kuskurenka sannan ka gane cewa abunda kayi sam bai dace ba, bawai nayi maka hakane saboda na ƙuntata maka ba, alokacin da Maimoon ta sanar mun cewa kai kayi mata ciki wallahi naji sanyi acikin zuciyata, kuma hankali na ba ƙaramin ƙwanciya yayi ba saidai ban nuna hakan a fili ba, babban tashin hankalina shine fargaban kar ta sanar mun cewa bakai kayi mata ciki ba, wallahi tallahi na tabbata inda a lokacin Maimoon ta ambaci wani ba kai ba, Da alokacin zuciyata bugawa zata yi kuma babu abunda zai hana na yanke mata maƙogaro, amma jin kaine zuciyata tayi sanyi sosai ma ..." Maimoon gaba ɗaya ta rasa gane kan Daddynta, kuma maganganunsa sunyi matuƙar ɗaure mata kai, ba ita ba hatta shima Doctor Hasheem yayi mamakin jin haka daga wajen Daddy, yana tunanin meye dalilin da yasa hankalin Daddy ya kwanta jin shine yayi mata cikin... Daddy ƙiran sunan Maimoon yayi sannan yace "kiyi haƙuri Daughter tsawon shekaru huɗu kenam na ɗauke miki farin ciki nah dalilinda yasa haka shine kasancewar Hasheem yana can prison hankalinsa ba'a kwance yake ba, taya Ni kuma zan sanya ki farin ciki? idan nayi haka banyi masa adalci ba, yanzu zan sanar muku sirrin da muka daɗe muna ɓoyeshi tsawon shekaru ashirin, babu wanda yasan wannan sirrin daga Ni sai Mahaifinka Hasheem sai kuma Mahaifiyarka da kuma Matata Mahaifiyar Maimoon gata nan a gefena, sai kuma Kakanunku waɗanda suka rasu tintini, sai kuma Yayan Mahaifinka dake ƙasar Niger...." yana kaiwa nan yaja dogon numfashi, Kowa ya baza kunnuwa domin jin wannan sirrin, Daddy ya cigaba da cewa "Hasheem tin kuna yara soyayya ta ƙullu atsakaninka da Maimoon, koda yaushe kuna tare hakan yasa muka yanke shawara Ni da Mahaifinka Alhaji Bukar na Aurar daku a lokacin, tin kana Ɗan shekara goma ita kuma Maimuna tana shekara biyar akayi muku Aure ba tareda kowa ya sani ba, sai iya mu, kuma abunda yasa bana fargaban komai akanku shine kun kasa rabuwa har Allah yasa kuka mallaki hankalin kanku, akwai waɗanda suka zo neman Auren Maimoon amma naƙi amincewa aciki harda ƴan uwanta, duk wanda yazo nakan koreshi saboda Auratayyar dake tsakanin ku, kuma itama Alhamdulillah bata tsayawa da kowa sai kai, bata ambatar ko wane suna sai sunanka, wannan shine sirrin da muke ɓoyewa yanzu kuma na bayyanar shi, saiku fara ɗaukan kanku a matsayin ma'aurata..." Doctor Hasheem cike da mamaki yake bin Daddy da kallo gaba ɗaya kamar babu rai a jikin shi, murya na kakkarwa yace "Daman akwai igiyar Aure atsakani na da Maimoon? kuma tin muna yara..?" Jinjina kai Daddy yayi yana kallonsa, kowa dake wajen yayi mamakin jin haka banda Ammy wacce itama tasan da maganar, Hawaye ne suka wanke mata fuska cikin kuka tace "Daddy a gaskiya ni yanzu bazan cigaba da son Hasheem ba, bana sonsa yanzu, inda a baya ne zanyi farin cikin jin hakan amma yanzu kam sam baya raina..." Ammy tace "banda abunki ai yanzu ne ya kamata ki soshi saboda yaron dake tsakaninku, kuma Ni a wannan lamarin nafi ganin laifinki shin meya kaiki ɗakinsa cikin dare?..." Daddy yace "ya isa haka banason taune-taune, abinda ya wuce ya wuce kenam tinda Allah yaso ba aikin alfasha suka aikata ba, kuma yaronsu ɗan sunna ne ba shege bane..." Ya kalli Maimoon yace "ke kuma duk abunda zaki faɗa bazaiyi tasiri anan ba, shin mekike nufi? kinaso kice mun a raba Auren? toh wannan labarin kuyange ne abunda aka ɗaura tin shekarun baya yanzu bazaki warware shi ba, nagaya miki ki cire wannan batun a bakinki, Hasheem mijinki ne har a lahira saboda haka ku sasanta kanku kafin nan da ƙwana biyar zaki koma gidansa ku cigaba da rayuwar ku acan da kuma yaronku..." Ya maido da kallonsa kan Lailah wacce tin farko kanta yake ƙasi jin an ƙira sunanta ne yasa ta ɗago tana kallon Daddy yace "ke kuma Auta abunda yasa ban tsayar muku da maganar Aurenku ba shine inaso sai Yayanki ya fito daga prison tukun, tinda Allah yasa kin kammala karatun N.C.E kuma Yayanki ya fito abunda ya dace shine ayi maganar Aurenki kema ki tare agidan mijinki, sannan na sama miki aiki a gidan redio, tinda ɓangaren da kika karanta kenam Journalist Koh?..." Dasauri ta ɗaga masa kai alamar ehh, Sannan ya kalli Doctor Mansur ya sanar masa cewa "tinda lokaci yayi abunda nakeso dakai Mansur shine ka turo magabatanka nan gidan, in yaso daga nan zamu wuce dasu can ƙasar Niger domin nema maka Auren Lailah a gurin Baffanta wato Yayan Mahaifinta wanda suke uwa ɗaya uba ɗaya shine kawai ya rage musu...." Doctor Mansur ya amsa cikin farin ciki...... ★★★★★★ Return to Ogah Junaid part★★ Washe garin safiyar Monday around 7:30 kowa ya hallaru akan dinning, Amreesh da Angel suna sanye da kayan uniform ajikinsu alamun school zasu tafi, ga kuma Hafzat itama, Junaid ne ya sauƙo daga stairs yana sanye da jallabiya ajikinsa sauƙowarsa kenam yaran suka fara gaishe shi suna faɗin "Good morning Daddy.." fuskarsa ɗauke da murmushi yace "morning my Child's, fatan kun tashi cikin ƙoshin lafiya..". suka amsa masa gwanin burgewa, ya kuma cewa "bana breakfast da sassafen nan amma saboda ku zan rinƙa breakfast da wuri..." Little Angel tace "meyasa Daddy?.." yace. "saboda kuna zuwa school Ni kuma nafison nayi breakfast da yarana masu albarka...". duk sukayi dariya, sai daga baya itama Hafzat ta gaishe shi duk suna zazzaune Oga ya kalli Amreesh yace "Momy where is your mother?..". tace "ai Daddy tana can tana shirya Yaya Areeph" yace "okay..." suna cikin wannan zancen sai gata ta sauƙo falo tareda faɗin "kuyi haƙuri na zaunar daku ban zuba muku abinci ba koh...". Junaid kansa akan wayar hannunsa yanata pressing ɗinta har ta gama zuba musu sannan ta ɗauki kular abinci zata nufi upstairs daiden lokacin da Junaid ya ɗago ya kalleta tareda faɗin "ina zaki kai kular?.." tace "Amm zan je nayi feeding ɗin Areeph ne shima ya kammala shirin school..." Abun ne yayi matuƙar ɗaure masa kai cike da mamaki yace "ban gane wannan wani irin bad behavior ne haka, shi bazai fito cikin ƴan uwansa yayi breakfast ba kenam? ke da shi your very stupidity, kizo ki ajiye kular ki ƙira mun shi..." Ayush jiki a sanyaye ta dawo ta ajiye kular fuska ba Annuri tana baƙin cikin yanda yake mata tsawa agaban yaranta, haka ta haura taje har ɗakin Areeph, kafin ta fito dashi saida tayi masa warning sosai akan in sunzo ya durƙusa har ƙasi ya gaishe da Daddynsa gudun kar ya fusata yace zai daki yaron, bayan sun sauƙo falo Areeph ƙin zama yayi yanata bayan Daddynsa daƙer ya buɗe baki yace "Good morning Daddy..." Juyowa yayi jin muryar Areeph ata bayansa alhalin bai san da zuwansa ba, yana kallon Areeph yace "haka ake gaisuwa a tsaye?..." bai bashi amsa ba saima ƙafe shi da yayi da ido, zaro ido Junaid yayi yace "ba magana nake maka ba?".. yayi maganar cikin tsawa domin har saida su Little Angel suka tsorita shima kansa Areeph saida ya tsorita sosai, cikin ƙanƙanin lokaci ya fara jin tsoron Daddynsa ganin baya masa da wasa, ƙanƙame Ayush yayi dake a gefensa take, tasowa Junaid yayi a fusace ya fizgo hannunsa tareda dokashi a ƙasin carpet, sai buguwar kansa kawai aka ji yayi gabbbb, hakan ma yasa hannu ya zabge shi da mari, dasauri Ayush tasa hannu akan kuncinta kamar ita aka mara, kamar zatayi kuka haka take ji, jin yanda Junaid yaketa zabga masa mari, Areeph ba abunda yake sai ihu yaji mazgar manya, shi tinda aka haife shi ba'a taɓa sa hannu an dake shi ba sai yau, Ogah Junaid bai daina dukan yaron ba saida yaji Angel da Amrish sun fashe da kuka ganin anata dukan ɗan uwansu tukun ya daina dukan a fusace rai a ɓace yake cewa "bazan juri ganin yaro ƙarami yana abu irin na marasa tarbiyar yara sannan na zuba masa ido ba, i'm a not crazy man...". ya ƙarasa maganar yana kallon Ayush ya kuma cewa "zan iya karairaya shi in har baki canza masa tsarin rayuwa ba, daga yau inaso na rinƙa ganinsa acikin ƴan uwansa, sannan dole zai rinƙa cin abinci acikin mutane, wannan tsaurin idon nashin zan caccaka su...". ya juyo kan Areeph yace "Kneel down..." Areeph a gigice ya tashi daga kwance zaiyi kneel, Ayush tana goge hawaye tace "bai ci abinci ba sannan kuma zasu makara a tafiya school..." wani irin harara ya wurga mata sannan yace "banga amfanin zuwansa school ba tinda ba'a koyar da tarbiyya, ya zauna a gida I'll teach him a lesson..." Bayan su Angel sun kammala breakfast ɗinsu wucewa sukayi suna kuka suka ɗaɗɗauki lunch bag ɗinsu, already akwai dreban su wanda yake kaisu makaranta sannan idan lokacin tashi yayi ya ɗauko su, a wannan ranar Areeph baije school ba, haka Junaid yake gana masa azaba kamar ba ɗansa ba, duk ya faffasa masa jiki da wayar nepah hakan ma ya cire masa kayan jikinsa gaba ɗaya daga shi sai pant yake zabga masa wayar, Ayush ganin bazata iya juran ganin ana azabtar mata da yaro ba yasa ta nufi ɗakinta ta rufe, itama Hafzat ba ƙaramin tausayin Areeph tayi ba, har da hawayenta, da gudu tazo ta durƙusa agaban Ogah tana roƙonsa cewa "dan girman Allah Uncle kayi haƙuri ka ƙyale shi haka, yayi ƙanƙanta sosai a irin wannan dukan, zai iya shiɗewa wallahi...". ta ƙarasa maganar tana kuka, kallon ta yayi yace "tashi ki bani guri..." jiki a sanyaye haka ta tashi itama ta nufi ɗakinta, Ogah Junaid saida yayi kwana uku yana azabtar da Areeph kuma yaƙi barinsa yaje makaranta, a waɗannan kwanakin itama Ayush ta daina kula Junaid ko gaisuwa bata haɗasu tasha kuka kamar ranta zai fita ganin yaron duk ya fita hayyacinsa, hakan yasa ta fice a gidan kai tsaye gidan Uncle Artaff taje takai ƙaransa, shima Uncle Artaff jin hakan yasa yayi gaggawar zuwa gidan, a lokacin da su Uncle suka shugo falon daiden lokacin Areeph ya faɗi ƙasi ko motsi babu, a rikice Ayush ta nufo gurin da gudun gaske tana kuka tareda faɗin "wayyo Allah na shiga uku ya kashe mun yaro..." Shima Uncle Artaff nufan gurin yayi yana salati hatta shima Ogah Junaid ya tsorita ganin yanda yaron ya yanki jiki ya faɗi, cikin gaggawa aka ɗauke shi sai hospital.... ★★★ Bayan ƙwana Biyar An kai Maimoon gidan mijinta daƙer Doctor Hasheem ya samu nasarar shawo kan Maimoon har ta haƙura, yanzu soyayyarsa ta dawo mata cikin zuciyarta duk da daman tana sonsa kawai tana masa wulaƙanci ne saboda abunda yayi mata amma daman bata daina sonsa ba, Doctor Hasheem yasa an gyara masa gidansa, an chancanza design ɗin gidan da penti gaba ɗaya komai ya dawo sabo, ga yaronsu yanzu yasan waye Babansa kullum yana manne a jikinsa, yanzu rayuwa ta canza musu ta dawo musu sabuwa, Doctor Hasheem kamar baiyi zaman prison ba, ya cika ya murmure haskensa ya dawo masa, yana ƙoƙarin bawa Maimoon kulawa sosai ita da yaronta, sannan kafin mommyn Junaid tabar Nigeria ta bar saƙo cewa da zaran Doctor Hasheem ya fito a prison a bashi letter cewa "ta bashi shugabanci a hospital ɗinta, shine mai kula da hospital sannan duk ma'aikatan hospital a ƙarƙashin jagorancinsa suke... Ita kuma Lailah an yanke ranar bikinta itama sauran sati Uku, ga ta samu aiki a gidan redio, rayuwa ta sauya mata, fitowar ta daga cikin ma'aikatansu kenam zata tari napep ya kaita gida, tazo tsallakawa bata ankara ba saiga wani ƙaramin jeep yazo ya ƙwasheta saida tayi sama tukun ta faɗo ƙasin ƙwalta, kayinta ba ƙaramin buguwa yayi ba, tin daga lokacin bata ƙara motsi ba, kafin kace mai mutane har sun taru, ba'a tsaya jiran kowa ba sai hospital... Doctor Hasheem ba karamin razana yayi ba jin abunda ya faru da Lailah, daman yana hospital yana duba majinyata yazo zai fita da gudu yaga ashe itama Lailah har an iso da ita, a rikice ya karɓeta sai cikin emergency room, Shima Doctor Mansur ba karamin ruɗewa yayi ba jin Lailah tana asibiti, ba shiri shima ya nufi hospital ɗin Doctor Hasheem ba abunda yake furtawa sai "innalillahi wa inna ilaihi raju'un ².." da haka har ya isa. kafin a ankara Daddy da Ammy da Maimoon har sunji labari suma ba shiri suka nufi asibitin, Lailah saida tayi ƙwana biyu tana kwance tukun Allah yasa ta farfaɗo, kafin ta gama buɗe ido bakinta ya fara motsi tareda faɗin "Yaya ka dena dukan Ogah Junaid dan Allah, meya maka hakane, zaka kashe shi fah...". Jin haka yasa Doctor Hasheem nufan gurin dasauri yana ambatar sunanta, Lailah ƙoƙarin tashi zaune take, Doct Hasheem ne ya ɗagota zaune yana kallon ta tareda cewa "Lailah kin gane ni?..." bugan ƙirjinsa tayi tana murmushi tace "haba Yaya idan ban tuna dakai ba shin wazan tuna, nifa ban manta komai ba..." Doct Hasheem yace "amma naji kina ambatar sunan Ogah Junaid shin kin sanshi ne?..." Lailah cike da mamaki take kallon Doct Hasheem tace "Haba Yaya taya zan manta Ogah Junaid, tsohon saurayina ne fah, shine mutum na farko dana so a rayuwata, amma Yaya nayi mamaki taya abubuwan baya suka dawo mun ƙwaƙwalwata? yanzu ina iya tuna komai abunda ya faru a baya, tayaya Yaya? shin ina Ogah Junaid fatan ya samu lafiya koh? amma Yaya inadai baka illata shi ba dukan da kayi masa, naji tausayinsa sosai, toh ina kuma Ayushert take kodai ta gudu kashe mommy datayi ta hanyar gobara, naje na bayar da dukkan rahotannin ta agidan rediyo, an kamata ne?..." Doctor Hasheem tsayawa yayi yana kallonta cike da farin ciki memory sense ɗin Lailah ya dawo mata, amma abun fargaba shine kar Lailah ta dawo da soyayyar Junaid cikin zuciyarta, Lailah murya na kakkarwa tace "Aunty Maimoon.." tana kallon wajen da Maimoon take zaune itama Maimoon tasowa tayi tazo har wajen gadon Lailah tace "Lailah your welcome..". Lailah tana kuka tace "Aunty Maimoon kiyi haƙuri da laifin da muka aikata miki..." kafin ta ƙarasa Maimoon tayi saurin toshe mata baki tareda cewa "abunda ya wuce ya wuce kenam, ki cigaba da tsara rayuwarki na yanzu, Ogah Junaid ki manta dashi kawai yanzu Aure zakiyi..." Lailah dariya tayi tace "daman ai kawai na tuno ne amma rayuwata ta yanzu tafi mun, a baya abubuwa marasa kyau na rinƙa aikatawa yanzu kuma Insha Allahu zan zamo uwa ta gari wa ƴaƴanta...." Duk sunyi farin cikin jin abunda Lailah ta faɗa, shima Doctor Mansur yana daga gefe har jikinsa yayi sanyi amma jin har yanzu Lailah tana tare dashi yasa ya sauƙar da doguwar ajiyar numfashi, shima ya nufi wajenta yana murmushi itama ganinsa yasa tace "mijina na kaina, kayi haƙuri lokacin da mota ta bugeni ina sauri ne zan koma gida shiyasa ban jira kazo ka ɗauke ni ba...". shafar gefen fuskarta yayi ba tareda yace komai ba sai murmushin farin ciki... Suma su Daddy da Ammy sunyi farin cikin dawowar sense ɗin Lailah.... suna cikin hirarsu sai sukaji an turo ƙofar ɗakin gaba ɗayansu kallon bakin ƙofar sukayi ganin yaro ya shugo, Doctor Hasheem yace. "kaii zo mana..". yaron yazo har gabansa ya riƙe hannunsa yana cewa "daga ina kake, meye sunanka?..." Rapeekh dake zaune saman cinyar Ammy yace "Laaaa Daddy shine Abokina wanda nake baka labarinsa class ɗin mu ɗaya dashi kuma kullum sai munyi faɗa...." Doctor Hasheem ya kalli yaron yace "kaine Areeph?.." Areeph dasauri ya ɗaga masa kai alamar ehh, ya tambaye shi meye full name ɗinsa, Areeph kamar bazaiyi magana ba daƙer ya iya cewa "Máahmud Junaid Khan..." Jin sunan abunda ya ɗaure wa Doctor Hasheem kai, cike da mamaki yace "sunan Babanka Junaid Khan Máahmud?...". dasauri Areeph ya ɗaga masa kai, Doctor Hasheem kallon Lailah yayi yace "wannan yaron Ogah Junaid ne..." A zabure Lailah tace "yaron Ogah Junaid kuma? Innalillahi haka yaran suka girma, yaushe ne mukaje hidimar sunansu...." suna cikin tattaunawarsu saiga Ayush ta shigo ɗakin kamar zata kife tayi sallama, duk suka juyo suna kallonta bayan sun gaisa tace "Areeph inata nemanka ban ganka ba...". Doctor Hasheem ne yace "Malama Ayushert your welcome...". cike da mamaki Ayush take kallon Doctor tace "Doct Hasheem kaine? Daman kana ƙasar?..." yace "wallahi kuwa ina Nam tsawon shekaru bamu sake haɗuwa ba" Zama tayi suka fara tattaunawa akan yanda rayuwa ta juya dasu, Doctor Hasheem ya kwashe labarin abunda ya faru dashi har zamansa a prison ya sanar mata, tayi matuƙar tausaya masa sosai, itama ta bashi labarin tafiyarta bayan tabar gidansa ta koma daji da zama har tayi zaman prison itama, Zaro ido Doct Hasheem yayi yace "kema kinyi zaman prison ne?...". tace "ehh amma zaman wata uku nayi kai kuma gashi har tsawon shekara huɗu...". Lailah tace "Aunty Ayusher..." Ayush ta kalli Lailah tace "Lailah ashe abunda ya faru dake kenam?..." ta amsa mata tace "toh Allah ya tsare gaba..." Duk suka amsa da Ameen... Doctor Hasheem yace "amma Ayush meya kawo ku hospital..." tace "wallahi satin mu guda a asibitin nan, na kawo Areeph bashida lafiya...". yace "Allah Sarki kinga kuma ina zuwa nima amma ban lura daku ba, nadai ga Ogah Junaid jiya shida Malam Lawan amma iya gaisuwa mukayi ban tambayesu abunda ya kawo su ba saboda naga suma sunada iko da asibitin ....". ya kuma cewa "toh amma meya same shi ne?..." Tace "Babansa ne yayi masa dukan mutuwa don har saida ya suma..." ta buɗe ma Areeph riga duk ta nunnuna musu yanda ya faffasa masa jiki... Girgiza kai Doctor Hasheem yayi sannan yace "innalillahi wa inna ilaihi raju'un irin wannan dukan ai yayi tsari a yaro ƙarami irin wannan, gaskiya Ogah Junaid bazai taɓa canzawa ba, har yanzu yana nan da wannan zafin ran nashin..." Lailah wani irin ƙololuwar baƙin cikine ya ziyarci cikin zuciyarta ganin yanda Ogah Junaid yayi wa yaronsa, ko kaɗan bataso taga ana dukan yaro, sam ba ƙaramin haushin shi taji ba... Kowa a wajen saida ya tofa albarkacin bakinsa.... Rapeekh yaron Doctor Hasheem yace "shiyasa bana ganinsa a makaranta yanzu, kuma a ajinmu an bamu result ɗin jarabawar mu na canjin aji, Ni nayo na ɗaya..." Ayush tace "kai kayo na ɗaya? shima Areeph an karɓo result ɗinsa shima na ɗayan yayo kuma abin ku ɗaya?..." Doctor Hasheem yace "ehh ajinsu ɗaya mana akwai wani malamin su yana gaya mun cewa dole sai an sake musu jarabawa a iya tsakaninsu domin kowannen su yanada ƙoƙari sosai sai anyi musu inter biyu..." Areeph ya kalli Ayush yace "mommy aini bazan taɓa faɗuwa a exam ba..." Shima Rapeekh yace "nima bazan taɓa faɗuwa ba..." A haka sukayi wasa da dariyarsu suka fice a ɗakin, A ranar aka sallami su Ayush suka koma gida, Masha Allah Areeph duk ya rage abubuwanda yake yi a baya, kuma tsoron Daddynsa ya ziyarci cikin zuciyar shi, duk abunda aka ce masa yayi da hanzarinsa zaiyi, Amma saidai har yanzu akwai wannan zuciyar da kuma idan aka masa magana baya saurin bada amsa wannan ajininsa yake amma akwai ladabi da biyayya yanzu kam.... Ana falo kowa yana zazzaune an kafa eyes akan plasman ana kallo, Ogah Junaid yana zaune Angel da Amrish kuma suna gefe da gefensa, Ita kuma Ayush tana ƙasin carpet sai sheƙar ruwan tea take fuska ba Annuri, daman hakane indai tana wajen da Junaid yake toh bata dariya, shima Areeph yana gefen mommynsa a zaune, Junaid banda satar kallon Ayush ba abunda yake, gaba ɗaya a takure yake ganin fushinta yaƙi ƙarewa, kuma tin daga lokacin daya fara dukan Areeph ta ƙaurace masa, yanzu kowa a ɗakinsa yake kwana, yana so yayi mata magana amma saidai ya kasa sai kuma take masa ƙwarjini ga yanzu ta ƙara girma sosai, komai nata a cike pamm, ganin bazai iya yi mata magana kuma yanaso ya rarrasheta ta bashi haɗin kai waren ƙwanciya ya kalli Areeph dake gefensa yace "Daddyna zo mana..". Areeph tashi yayi yaje gabansa yace "gani...". ya shafa gefen fuskarsa yace "Daddy kana fushi dani ne?.." girgiza kai Areeph yayi alamar a'ah, Ogah yace "toh kayi haƙuri kaji koh! Insha Allahu bazan ƙara dukan ka ba amma kar ka ƙara yin laifi kaji koh?...". Areeph yace "Daddy bazan ƙara ba". Yace "kace a mommynka itama tayi haƙuri ta yafe mun..." Areeph yaje gaban Ayush yace "mommy kiyi haƙuri ki yafewa Daddy yace bazai ƙara dukana ba...". Shuru Ayush bata bashi amsa ba, sai shan shayinta take, bata ankara ba taji an karɓi cup ɗin hannunta, dasauri ta waiwaya tana kallon Ogah Junaid, shi kuwa ajiye cup ɗin yayi akan table ɗin falon sannan ya sauƙo ƙasin carpet shima suka jeru tareda riƙe haɓarta yace "my sweetheart har yanzu fushi kike dani? ko yanzu kin wahalar dani please my..." Ayush kawar da kanta tayi gefe, ya kuma cewa Mommy ta aikoni gurinki akwai saƙonda zan gaya miki..." daƙer take motsi da lips ɗinta tace "meyasa tinda kazo baka gaya mun ba.." Yace "Noo na manta ne amma yanzu tashi muje bedroom saina gaya miki koh.." tace "meyasa baza'a gaya mun anan ba" yace "bakiga da yara bane". turo baki tayi tareda miƙewa tsaye ta nufi upstairs, shima bin bayanta yayi dasauri, Su kuwa yaran basu kawo komai aransu ba sai suka cigaba da kallonsu, bayan shigar su bedroom rufe ɗakin yayi tareda murɗa key, cike da mamaki tace "yada rufe ɗaki kuma ...". takowa yayi yazo gabanta yana ɗan rera waƙarsa ta soyayya yasa hannu ya jawota jikinsa yana shafeta, tace "wai meye hakane, Ni ka ƙyale Ni, hakan ne saƙo ko?...". yana lumshe ido yace "Ni mijinki ne bai kamata ki ƙaurace mun ba, don haka saƙon Baby zan ajiye miki anan..." ya ƙarasa maganar yana shafa marar ta. Zaro ido tayi tace "meeee cab ɗin, ban shirya karɓan new Baby ba don haka kaban guri na wuce ...". Junaid ƙara rungumarta yayi yana kai mata kiss a ko ina na sassen jikinta...". Ita kuwa ƙoƙarin ture shi take tareda faɗin "kai da kayi shekara huɗu kana zaman kaɗaici shin mutuwa kayi ne?...". ta ƙarasa maganar daiden lokacin daya ƙwantar da ita akan gado, cikin dabara da ƙwarewa duk ya zamar mata da kayan jikinta shima ya cire nashi, ya jawo musu mayafi gaba ɗayansu..... Sanadiyar wannan saƙon ne ya kawo musu sasanci da maslaha a tsakaninsu, komai ya wuce.. ★★★ Washe gari za'ayi jarabawa a tsakanin Areeph da Rapeekh aciki za'a zaɓi gwarzo kenam wanda yayo na ɗaya da kuma na biyu acikinsu, kowa yazo school da niyar cinye exam acikin Babban hall na makarantar, kowa da wajen zamansa domin akwai rata sosai a tsakanin Areeph da Rapeekh, security ɗaya aka ajiye musu wanda zai rinƙa yawo akansu, only one hour kawai aka basu, tinda suka fara rubutu babu wanda ya ɗago da kansa, Areeph burinsa shine yaga ya wuce Rapeekh a ilimi da komai, bayaso su rinƙa yin bracket... Haka shima Rapeekh yafi son yazo na ɗaya a duk class ɗinsu in yaso Areeph yazo ana biyu, kowa yana kishi da kowa... Hakan kuma ba ƙaramin burge malaman makarantar suke ba saboda kishi akan karatu abu ne mai kyau, After 30 minute saiga Rapeekh ya tashi tareda miƙawa security takardarsa har ya gama nashi exam, Ganin haka ba ƙaramin razanar da Areeph yayi ba, kawai tsayawa yayi yana kallon Rapeekh cike da mamakinsa har ya gama kuma duk questions iri ɗaya ne, ƙirjin Areeph ne ya soma harbawa kamar zaiyi kuka shi har ya saddaƙar cewa ya faɗi a exam ɗin nan, duk da yasan amsoshin gaba ɗaya toh amma saurin fitar Rapeekh ne ya karyar masa da gwiwa, yana cikin tunani yaji security ya dafa kafaɗarsa yana cewa "too pass Areeph remain 15 minutes...." Areeph miƙa masa takardar yayi yana shirin tashi security yace "ha'a ya baka ƙarisa ba?..." Hawaye ne suka fara gangarowa Areeph, security ya rarrashe shi tareda ƙarfafa masa gwiwa har ya ƙarisa exam ɗin shima ya fice jiki ba ƙwari, Areeph ba haka yaso ba, baiso ace Rapeekh ya riga shi zana exam ba.... tinda Areeph ya koma gida bai samu kwanciyar hankali ba, abinci ma kasa ci yayi gaba ɗaya Ayush ta shiga damuwa ganinsa tinda ya dawo yake ta kuka, kuma ya kasa gaya mata abunda ya same shi, haka akazo yin night lunch nan ma ya kasa cin komai sai a lokacin Daddynsa ya fahimci akwai matsala a game da yaron, ya jawo Areeph jikinsa yana tambayarsa abunda yake damunsa, nan Areeph ya fashe da kuka yana faɗin "Ni nasan Rapeekh ne zai cinye jarabawar..." Junaid yace "meyasa? bakayi ƙoƙari bane? kodai ka manta wasu abubuwan ne?...". Areeph yace "ban manta komai ba duk na rubuta su, Rapeekh ɗin ya rigani gama exam ɗin..." Dariya Junaid yayi sannan yace. "hakan ba shi yake nuna cewa baza kaci exam ba, ko mutum ya gama da wuri indai bai rubuta daidai ba toh bazai ci ba, don haka ka ƙwantar da hankalinka okay .." Areeph ɗaga masa kai yayi sai yanzu hankalinsa ya kwanta, Ayush tace "Ni wallahi har ka tayar mun da hankali, nayi tunanin wani abu ne...". Junaid ya kalleta sannan yace "ehh ai dan ke baki shiga class bane shiyasa baki san muhimmancin karatun ba ...." turo baki Ayush tayi tace "abun harda gori ne? Naji amma ai waɗanda sukayi bokon ma babu abunda zasu nuna mun tinda nasan kalmar baƙi da fari.." taɓe baki Junaid yayi yana kallonta yace "toh ja da yellow fah?.." turo baki tayi rai a ɓace ko kallonsa bata yi ba, ya kuma cewa "yarinyar nan babu yanda banyi dake ba akan ki shiga school amma kika ƙi ai da yanzu an nema miki aikin yi..." ta juyo tana kallonsa tace "babu abunda ban iya ba..." Yace "eh kin iya ƙwanciya kiyi bacci ba, girki ma ba wani iyawa kikayi sosai ba, ai duk zan sallami ƴan aikin nan domin a takure nake bana iya cin girkin su..." Little Angel tace "Daddy daman mommy bata shiga school ba?..." Amreesh tace "shiyasa ranar nace tayi mun Assignment ɗin Mathematics taƙi mun sai Aunty Hafzat ce tayi mun...." Areeph yace "Ni daman nake yin Assignment ɗina da kaina, toh meyasa mommy bata je school ba? sai kace forest girl..." Angel ta kuma cewa "wata ƙila forest school tayi..." duk yaran suka kwashe da dariya harda shi kansa Junaid, Ayush kuwa ta ƙulu har ta kusan fashewa tsabar kumburi, Amreesh tace "daman fah forest habitat ce fah...". Areeph ya kalli Ayush yace. "La la la laaa daman mommy ke ƴar forest District ce?..." kuma du suka ƙara tintsirewa da dariya, dasauri Ayush ta ɗauki wayar wutar nepa ta nufo wajensu tana faɗin "ina dai Ni Abokiyar ku ce ko?..." duk su ukun suka rufu akan Ogah Junaid suka ihu tareda ambatar sunan "Daddy! Daddy!! Wayyo Daddy!!!..." Junaid riƙo hannun Ayush yayi tareda jawota jikinsa yana faɗin "kiyi haƙuri mommy wasa suke miki dai ..". zamar da kanta tayi ta nufi upstairs tana gunaguni... Da haka suka sha hirar su har kowa ya wuce ɗakinsa, yau kam Ogah da kansa ne ya gyarawa yara waran ƙwanciyarsu ya tottofa musu addu'a duk da suma sun iya haka suka shafa ya rufesu da mayafi sannan yasa key a ɗakin, shima Areeph haka akayi masa tukun Ogah ya wuce ɗakinsa da Ayush ɗinsa .... Washe gari yau iyayen Judan daga ƙasar Jidda suka zo Nigeria neman Auren Hafzat, shi kuwa Judan ƙasar da yake aiki kuma ƙasar california ne, daga Abuja ne suka nufi garin Kano gurin iyayenta har da Junaid shima, Masha Allah kuma an karɓesu hannu bibbiyu a lokaci ɗaya aka yanke ranar da za'ayi bikin, Iyayenta abun ya basu mamaki daga zuwa neman Aure sai kuma a yanke ranar Aure? Amma dake sunga manya-manyan kuɗaɗe da hanzarinsu suka yanda, an yanke ranar sauran sati biyu ɗaurin Aure... Ranar da za'ayi na Lailah da Doctor Mansur..... A yau ne Ayush ta raka Areeph school ɗinsu domin karɓan result ɗinsa, tana ta addu'a Allah yasa kar Areeph ya faɗi a jarabawar, Shima Rapeekh yazo karɓan tasa shida Abbansa, anan suka sake haɗuwa da Doctor Hasheem da Ayushert, amma wannan karan kam iya gaisuwa ne ya shiga tsakaninsu, Kowa an bashi result ɗinsa a wannan karan ma Bracket suka sake yowa duk sun cinye... Duk babu wanda yaji daɗin hakan a tsakanin Areeph da Rapeekh, amma saidai an sake basu wata dama kuma du na sake yin exam amma wannan karan exam zai kasance Verbal expression ne, wato magana ta Turanci har tsawon awa guda acikin bainar jama'ar malamai da kuma ɗaliban makantar da kuma iyayensu sauran nan da ƙwana uku za'ayi... Duk wanda ya ƙafe toh ya faɗi, kowa an bashi takarda mai tsawon rubutu na English zasu je su haddace amma kowa da nashi salon yanda zai gudanar, ba iri ɗaya bane rubutun, kamar debate kenam.... Kowa acikinsu sai ya ɗau yin murmushi alamun bazai gagaresu ba... A cikin kwana uku nan kowa yayi bita sosai, sun haddace wannan rubutun paper gaba ɗaya da temakon iyayensu, domin kusan kwana suke suna karatu, Areeph Daddynsa ne yake taya shi karatun, har kusan kwana suke suna karatun, ita kuwa Ayush bata ma arai ba domin bazata iya kwana tana taya yaro karatu ba, tinin bacci yake ɗaukanta... Shima ata ɓangaren Rapeekh Abbansa ne yake tayashi karatun, Yau ake ranar Debate kowa ya hallaru, ga part ɗin malaman makarantar daban, part ɗin ɗalibai daban, haka kuma part ɗin iyayen ɗaliban suma daban, ga kuma gurin da masu gasar zasu tsaya, Rapeekh ne first ɗin ƙira ya fito, yaron ya fito da zafinsa saida ya fara gabatar da kansa tukun ya fara sabarbaɗo turanci masu ma'ana, kuma yabi kan ƙa'idojin rubutun idan akazo wajen comma saiya dakata haka yaɗau tsawon awa guda tukun ya tsaya a gurin p-stop tukun nan ne kuma ƙarshe, yaron yasha tapi agun al'ummar wajen, kowa yabon Rapeekh yake, kuma ya burge mutane da yawa, ba ƙaramin ƙoƙari yayi ba, karatun turanci kamar a bakinsa aka ƙera shi, Abbansa da Mamansa murna kamar bazasu mutu ba, da sauran ƴan gidan Daddy da Ammy da kuma Lailah duk sun halarci gurin... Anzo kan Areeph kuma jikinsa ne yayi sanyi ganin yanda aketa tapawa Rapeekh, gani yake kamar bazai samu masoyan da zasu tapa masa har haka, wasu har da hura wusir wasu kuma ihun farin ciki suke acikin ɗaliban, abunda yasa jikinsa ma ya ƙara yin sanyi saboda Rapeekh daman ya fishi masoya domin yaro ne mai faran-faran acikin mutane, kowa nashi ne, shi kuma Areeph sam baya shiga cikin mutane balle su shaƙu, amma bai damu da wannan ba saboda kowa ƙoƙarinsa ne zai fidda shi bawai yawan mutane ba, ƙiran sunan Areeph aka dinga yi amma yaƙi fitowa, Ogah Junaid kamar ya nitse ƙasi haka yake ji gashi gurin zamansu ba ɗaya ba balle yasa shi dole ya fita, Ayush Addu'a ta shiga yi masa ido a rufe, wasu daga cikin ɗaliban har sun fara cewa "Rapeekh ne ta cinye shine yayo na ɗaya, gashi Areeph kam saboda bai iyaba ya kasa fitowa...". haka wasu suka shiga yimasa dariya, Areeph kansa a sunkuye ko ɗagowa beyi ba balle yayi niyar fitowa, saida shugaban makarantar ya tashi yaje har gabansa yace "Areeph meya farune ka kasa fitowa kodai bakayi karatu ba?...". shuru baiyi magana ba, akayi dashi ya fito yaron nan yaƙi, Ogah Junaid zuciyowa yayi ya miƙe tsaye zai bar makarantar Ayush tayi saurin riƙo hannunsa kanta a sama tana kallonsa tace "dan Allah kar ka tafi ka barshi a wannan halin, kaje ka same shi kaji meye matsalarsa na roƙe ƙa..." zamar da hannunsa yayi ba tareda ya furta komai ba ya nufi yanda Areeph yake a zaune still kansa a ƙasi ya kasa ɗagowa, Junaid durƙusawa yayi a gabansa ya riƙo hannun Areeph sai a lokacin yaji tsananin tausayinsa ya kama shi, a hankali ya furta sunansa "Areeph...." Jin muryar Daddynsa yasa ya ɗago kansa a hankali suka haɗa ido gaba ɗaya fuskarsa ya jagwalgwalewa da hawaye, har idonsa ya canza launi, Junaid ya cigaba da cewa "kada ka karaya yaron kirki, kaima ka fita da zafinka insha Allahu zakayi nasara, ragon namiji ne yake karaya dayin abu, ka tashi ka fita kamar Damisa kaje duk ka hargutsa taron da zazzafan turancin ka, jarumi na tashi mana, kar rashin yin baccin mu ya tashi a asara please my Son...." Lokaci guda Areeph yasau ƙayataccen murmushi tareda goge hawayen fuskarsa ya tashi shima ya fita gaban taron, fitowarsa shima aka fara masa tapi tin kafin ya fara magana, hakan ya bashi ƙwarin gwiwar soma gabatar da kansa sannan yayi gaisuwa ta yaren turanci daga nan ya miƙi maganar sa har yanda ya dosa, shima ba ƙaramin turanci yayi ba, kamar ba ɗan Nursery school ba, hakan ma ba a Nigeria ba, domin shima Areeph yayi masoya sosai jin yanda yake suburbuɗo turanci shima har yakai ƙarshe, ihu da tapi kamar baza'a daina ba, Wannan result ɗin da za'a basu tin daga yanzu kowa zai karɓi sakamakonsa, Areeph da Rapeekh kowa acikinsu yana ɗaukin a bashi sakamakonsa domin ya duba marking nawa ya samu, Cikin rashin sa'a sai sukaga D same marking again, yanzun ma Bracket ne... Haushi kamar zai illata Areeph har da kukansa, shima Rapeekh kuka yake saboda baiso haka ba.... (ikon Allah yanzu acikinsu babu wanda zaije ƙasa yabarwa wani kenam?....) Areeph suna komawa gida da ƙatuwar jakarsa yayi gudu ya shige ɗakinsa yasa sakata, A ranar wuni yayi a cikin ɗakin bai fito ba har dare, Ayush ta bubbuga ɗakin tana ƙiran sunansa amma yaƙi buɗewa, shi wai yayi fushi ne hakan, Shima Junaid yayi ya buɗe amma yaƙi har Junaid ɗin ya haƙura yace "yunwa ma zata fito dakai ai..." har duk suka kwanta, cikin dare Ayush tazo bakin ƙofar tana bubbugawa a hankali tareda ƙiran sunansa amma yaƙi buɗe wa har zuwa yanzu, A haka har akayi tsawon kwana uku amma Areeph bai buɗe ba, Gaba ɗaya hankalin Ayush ba ƙaramin tashi yayi ba, tayi kukan har ta gaji, abun da tsoro ace yaro ya rufe kansa har tsawon kwana uku ɓaci ba sha, har ta saddaƙar da ya mutu a ciki, tsawon wannan kwanakin itama batasa komai a cikinta ba, Ogah Junaid yayi da ita akan taci abinci amma taƙi sai cewa take "taya yarona baici komai ba kuma Ni na ci impossible wallahi..." tayi tayi da Junaid akan yasa a ɓalla ƙofar ɗakin a dubo mata yaro amma shima yaƙi sai cewa yake. "ki barshi yunwa zata fito dashi..." tana kuka taje ta samu ɗaya daga cikin Bodyguards ta ƙirashi akan yazo ya ɓalla mata ɗakin Areeph, amma Ogah Junaid yaƙi barinsa ya shugo masa ɗaki, ganin babu abunda zata iya yi yasa ta faɗi ƙasi tana ihu na gaske, Hafzat itama kuka take saboda ba'a San halinda Areeph yake ciki ba, Angel da Amrish ganin yanda Mommynsu take ihu yasa suma suka fashe da kuka, ★★★★★ *DAY 4* Ogah Junaid ya shirya yau zaije ziyartar abokansa can headquarters, kwatsam saiga Ayush ta dirƙo a gabansa kamar wata mai Aljanu duk tabi ta rarrame tayi duhu yana shirin fita tasa hannu taci ƙwalar rigarsa, zaro ido yayi yace "what? Yushert kinsan abunda kika aikata kuwa?..." tana harararsa tace "abunda yafi haka ma zanyi maka indai bakaje ka buɗe mun yaro ba..." Girgiza kai yayi sannan yace. "Ni na kulle shi ne?...". Tace "idan bakai ka kulle shi ba ai key ɗin ɗakunan gidan nan a hannunka suke meyasa baza kaje ka buɗe ba, nasan yanzu haka ya fita hayyacinsa in ma bai mutu ba...". ta ƙarasa maganar tana kuka.. ganin yanda taci kwalarsa yace "ok muje to na buɗe ɗakin .." yayi hakan ne saboda bayaso raini ya shiga tsakaninsu kuma daman yau yanada niyar buɗe ɗakin.... Binciko key ɗin ɗakin yayi suka nufi ɗaikin Areeph, Ayush kamar zata kife tsabar gaggawa, suna isa gurin yasa key ya murza ƙofar saiga ɗakin ya buɗu, Ganin Areeph yasa Ayush razana ta zaro manya-manyan idanuwanta baki a sake tana kallon wajen da Areeph yake, Shi kuwa Areeph yana nan zaune saman gadonsa duk ya ɓata ɗakin da ledar Cake dasu Biskit da lemon juice dasu Bobo, har da Nutric Milk, duk yanda ya cicci su da shaye-shayen lemuka kala-kala, Yanzu ma haka yana kan tsakiyar gadonsa yana kan cin Cake ga lemon juice a gefensa yanda yaketa korawa, da zarar yaji bacci saiya kwanta yayi baccinsa, ga toilet ɗinsa a cikin bedroom bashida wata matsala .... Ayush dasauri ta kalli Ogah Junaid wanda shi kuma ya jingine kansa da jikin ƙofa sai dariya yake tayi domin tin farko yasan lokacin da Areeph ya jijjido waɗannan abubuwan ciye-ciyen kawai dai yayi shuru ne, kuma dalilin da yasa bai damu ba kenam.... Kallon Ayush yayi yace "meye kike kallona, ke kin hana cikinki abinci shi kuma yana cikin ɗakinsa wuni yake yana ci da sha idan ya gaji ya kwanta yayi bacci, duk a cikin fushin ne ..." ya ƙarasa maganar tareda barin wajen yana faɗin "nidai na fita saina dawo....." Gobe za'a sake yiwa Areeph da Rapeekh jarabawa again amma saidai wannan exam ɗin akan Mathematics ne masu zafin gaske duk wanda yaci acikinsu shine gwarzo kuma akwai kyaututtuka na musamman, Wannan karan kam dole ɗaya zai faɗi ƙasi, bazasu iya cinyewa gaba ɗaya ba, koda basu cinye gaba ɗaya ba amma da zarar ɗaya ya wuce ɗaya da marking ɗaya toh shikenam shine wanda ya cinye.... (Toh pah Su Areeph masu fushi😂😂😂))))...... (Toh kuma yanzu dai ware zaici wannan exam ɗin. Sai Allah,) Ina masoyan Areeph Ina kuma masoyan Rapeekh?? Su fito suyi magana..... 𝑡𝑦𝑝𝑖𝑛𝑔✍️ 𝗠𝗔𝗧𝗔𝗥 𝗗𝗔𝗠𝗨𝗦𝗔 the wife of a tiger🐅🐅🐅🐅 𝙼𝚊𝚕𝚕𝚊𝚔𝚒𝚗 𝙰𝚜𝚖𝚎𝚎𝚝𝚊𝚑 ✍️✍️ 𝙿𝚊𝚒𝚍 𝚋𝚘𝚘𝚔 𝚌𝚊𝚕𝚕 𝚘𝚛 𝚠𝚑𝚊𝚝𝚜𝙰𝚙𝚙 09065443871 *💫💫{{N W A}}💫💫* Book two C̶h̶a̶p̶t̶e̶r̶ 91 to 95 Da gudu Ayushert ta ƙarasa shugowa cikin ɗakin tana ambatar sunan Areeph tareda faɗin. "Areeph yarona kana lafiya, ka tsoratar dani sosai, meyasa zaka azabtar da Mommynka haka, nayi kewar ka..." ta rungumo shi tana kuka, shi kuwa Areeph sai ƙara tura biscuit yake a bakinsa, yace "Mommy ni inason na cinye Rapeekh a jarabawa...". Ayush tace "ka kwantar da hankalinka gobe za'ayi muku jarabawar Mathematics, kuma inaji araina kaine zaka cinye, amma kar ka sake rufe kanka a ɗaki kaji ko?..." Areeph ya jinjina kai yana kallon Ayush, ita kuma ganin biscuit da lemon baja² yasa ta ɗauka ta ɓare tana turawa a bakinta kamar kuncen yunwa, domin ba ƙaramin yunwa take ji ba.. Ogah Junaid wuce wa yayi headquarter zai kai musu ziyara, an daɗe ba'a haɗu ba, kuma zuwa wani satin zai bar Nigeria, sunyi farin cikin ganinsa sosai... A washe gari Areeph da Rapeekh sun zana exam ɗinsu na Mathematics kuma shine na ƙarshe, Mathematics yayi wahala sosai domin duk cikinsu babu wanda kansa bai ɗau zafi ba, don ko ɗan jami'a iya kacin exam ɗin da za'a masa kenam, duk da babu wanda ya cinye jarabawar gaba ɗaya amma an samu wanda ya fi ɗaya da marking ɗaya, saida akayi tsananin bincike akai tukun aka samu cewar Areeph yafi Rapeekh da marking ɗaya da rabi, ai kuwa a ranar Areeph farin ciki kamar kamar dai, Rapeekh shima duk da baici exam ɗin ba amma yayi farin ciki sosai ganin yanda Areeph yaketa tsalle yana murna shima saiya tsinci kansa cikin murnar abokin takararsa ya samu abunda yake so, sam Rapeekh baiyi baƙin ciki ba, saima taya shi murna da yayi, da haka har aka bawa Areeph kyaututtuka manya², shima Rapeekh an bashi wani abu amma bai kai wanda aka bawa Areeph ba, Shima Areeph acikin kyaututtukan daya samu ya raba biyu ya bayarwa Rapeekh rabi shima ya riƙe rabi dake yaran ba masu son abun duniya bane, sunada dukiya sosai shiyasa basu wani damu akan kyautar ba, burinsu shine ɗaya acikinsu yafi ɗaya marking shine gwabzawar da suke tayi.... ★★★★★★ Part of the kingdom.. Babban masarautar sarki Raamud ba ƙaramin tsaruwa yayi ba, domin an ƙara tsara shi, an mayar da masarautar part biyar, part ɗin farko shine yake ɗauke da Babban fadar sarki, daga nan za'a wuce cikin falon sarki Raamud da manya-manyan kujeru masu kyan gaske, ga babban plasman a manne da bango da wani glass table a tsakiyar kujeru, ta gefe guda kuma ƙaton dinning table ne da kujerunsa guda 12 a jere, daganan sai upstairs mai part biyu hagun da dama, upstairs na dama shine zai kai ka har bedroom ɗin sarki Raamud, upstairs na hagun kuma zai kai ka ne har ɗakin mommy.... Part na biyun gidan kuma saika wuce fadar sarki tukun a ƙara buɗe gate na biyu shine zai kaika part ɗin Ogah Junaid da iyalansa, kamar yanda na sarki Raamud yake haka shima nasu yake, daga nan sai anyi tafiya mai nisa an sake buɗe wani gate na uku sai kuma part ɗin Uncle Artaff wanda aka tanadar masa tinda shima yanada gado acikin masarautar shima kamar yanda aka tsara nasu part ɗin haka akayi wa nashi, daga nan sai babban hospital dake cikin masarautar wanda a wannan part ɗin Narasimha yake, shine mai musu magani da zaran basuda lafiya, sai kuma wani part na wasan yara, da kuma wajen buga ball, acikin masarautar akwai wani gate na ɓangare guda wanda ana buɗe shi sai lambun kayan fruits da vegetables da bishiyoyi mango da casho da banana da sauran abubuwa, A wani part kuma akwai gate ɗin da idan aka buɗe wajen ma'ajiyin Dokunan sarakuna ne da wasu kayayyakin yaƙi, ga ta ɓangare guda kuma jerukan motoci ne na alhurma kala-kala... Ga wasu karnukan turawa da aka zuba a kowani part na cikin masarautar, masu gadin masarautar kuma wasu manya-manyan sojojin Amurkawa ne da turawa, ga wasu munanan Bodyguards masu ƙarfin gaske da manya-manyan bindigunsu, mata masu ayyukan gidan, an nemosu ne ba ragwaye ba. Waɗanda kullum suna cikin Aiki, Mommy ko ɗaga tsinke batayi acikin masarautar nan, komai yi mata akeyi da umarnin Sarkin amma ba'a son ranta ba, saboda ita ta saba da motsa jiki da wasu ayyukan gida, mommy tayi ƙiba sosai ta ƙara fari kamar jini zai fita, tayi kyau matuƙa, duk abunda take buƙata kuwa dasauri ake mata, duk wani kulawa tana samu a wajen sarki Raamud, domin ba ƙaramin ƙaunarta yake yi ba, baya ƙaunar ganin ɓacin ranta..... Yau ranar Monday Around 12AM na dare. Mommy tana ɓangaren ɗakinta ita kaɗai ta tashi tana salati tareda jero addu'o'i daƙer ta tashi akan bed ɗinta ta nufi hanyar fita, kai tsaye downstairs ta sauƙo falo, daga nan ta nufi wani ɗakinta na magungunuwa taje ta ɗauko boxes sannan ta haura saman ɗakinta, tana shiga bedroom ta shige toilet, saida tayi kusan awa guda acikin toilet kafin na fara jiyowa kukan jariri, Ni Asmeetah ina daga bedroom abun ba ƙaramin bani mamaki yayi ba, ina tsaye sai kuma na ƙara jin kukan jariri kuma du, kafin kace mai sai muryoyin jarirai suka fara kuka a jere a jere, banyi gaggawar shiga cikin toilet ba, na cigaba da tsayuwa can sai naga ta buɗe ƙofar toilet, cike da mamaki da kuma son ganin abunda ke faruwa na zurawa ƙofar ido ƙwatsam sai naga mommy ta fito hannunta riƙe da jarirai biyu, tazo ta kwantar dasu saman gado daman ta rigada ta yanke musu cibiya ta wanke su tas, ta buɗe wardrobe ɗinta ta ciro kayan jarirai na sanyi farare masu kyau, duk ta sassanya musu ta feshe su da turare masu ƙamshin gaske wanda bazai cutar dasu ba, still ta kwantar dasu ta lulluɓe su, acikin wannan daren ta sake shigewa cikin toilet ta haɗa ruwan zafinta na gaske tayi wanka ta gyara cikin toilet ta feshe da turare yanda bazaiyi ƙarnin jini ba, ta wanke kayanta wanda ta ɓata, ta shirya kanta tsab itama ta gama feffeshe jikinta da turare da duk gaba ɗaya ɗakin, sannan ta tottofa wa jariran addu'o'i ta ƙwanta gefensu har zuwa sallar asuba... Har gari ya waye sarki Raamud bai san mommy ta haihu ba, hatta suma ma'aikatan gidan mommy ta hanasu shiga cikin ɗakinta a yau, bata sanarwa kowa ba, kuma dake ɗakinta yana saman Upstairs ba kowa ne zai iya jiyowa kukan jariran ba, Dalilin yin haka shine haihuwar nan ba ƙaramin kunyata mommy yayi ba, ita har cikin zuciyarta bata so ta haihu a halin nan ba, saboda a cewar ta bai dace ace yaranta suna haihuwa itama tanayi ba, taso ace tabar musu haihuwan ita kuma ta haƙuri amma saidai sarki Raamud ne ya tsayar mata akan cewa dole saita haifo masa wasu yaran, hakan yasa ta haƙura tabi umarninsa, shine dalilin da yasa yanzu ta haihu kuma ta gagara sanarwa kowa, Saida wata daga cikin kuyangen tazo zata ƙonƙosa ƙafar ɗakin mommy taji kukan jariri, da gudu ta juya baya bata tsaya a ko ina ba sai a ɓangaren sarki Raamud, tana zuwa ta durƙusa a gabansa tana maida numfashi tace "mai martaba sarauniyarka ta haihu naji kukan jariri acikin ɗakinta..." Sarki Raamud bai tsaya jin ƙarashen maganar ba ya miƙe tsaye da hanzarinsa ya nufi hanyar fita kai tsaye part ɗin mommy ya nufa, yana zuwa ya tura ɗakin yaji a rufe ta ciki, bugawa ya soma yi da ƙarfi yana ƙiran sunanta, daƙer tazo ta buɗe masa cikin jin kunya kanta a sunkuye, sarki Raamud kamar zai tashi sama tsabar farin ciki, cike da mamaki yake bin jariran da kallo sai kuma ya ɗago ya kalli mommy gaba ɗaya har shirin zaucewa yake tsabar farin ciki, dasauri yakai hannu ya rungumo mommy sosai kamar zai mayarta cikinsa, tsawon shekara uku taƙi haihuwa sai a wannan lokacin, nan ma saboda ta farantawa sarki ne yasa ta haihu, yana cikin godewa Allah yaji tace "dan Allah ina neman alfurmanka mai martaba .." juyowa yayi cike da farin ciki yace "ki faɗi duk abunda kike so zanyi miki Sarauniyata...." Tace "dan Allah inaso ne kar a sanarwa su Junaid cewa na haihu, Ni kar a sanarwa kowa ma, dan Allah...." Sarki Raamud yace "indai abunda kike so kenam shikenam nayi miki Alƙawari bazan sanarwa kowa ba saidai su zo su tarar dake da ƴaƴanki..." Kallonsa tayi sannan tayi murmushi, yace "amma zaki ban mamaki, taya kika haihu ke kaɗai? Sannan ba wani jikkata ko rashin lafiya a tattare dake?" tayi murmushi sannan tace "ikon Allah kenam, haka Allah yaso dani..." Shima yayi murmushi yakai Idonsa kan yaran yace "Masha Allah duk mai aka samu?.." Mommy tace "Namiji da kuma Mace..." Sarki Raamud lokaci guda kuma sai yake jin hawaye yana shirin gangaro masa saboda ya tuno da Bara'at uwar Ayush, itama twins ne a cikinta akazo aka salwantar dasu tareda mamansu sai kuma gashi Allah ya maido masa su ata ɓangaren mommy, Zama yayi ya ɗauki yaran ya tottofa musu addu'o'i sannan yace "na sanya wa yaron suna Artaff wato mai sunan Uncle Artaff (malam Lawan)... Macen kuma na sanya mata suna Bara'at..." Mommy taji daɗi sosai dajin sunan da ya sanya musu.... ★★★★★ Ranar Bikin Hafzat da Judan kowa acikin danginsa sunzo ɗaurin Aure har shima kansa Judan, sarki Raamud shima yazo Nigeria amma banda mommy, ita mommy abunda ya hanata zuwa shine jariranta waɗanda suka ci sati guda a duniya, itama Hafzat ta koma Kano domin daga can za'a ɗaukota acikin ƴan uwanta... Itama Lailah aranar aka ɗaura mata Aure ita da Doctor Mansur ɗinta, an kaita gidan mijinta cikin ƙoshin lafiya. Itama Hafzat aranar aka sata a jirgi sai ƙasar Jidda ƙasar su judan kenam, anan zata zauna... Ayush ba ƙaramin kewar Hafzat tayi ba, ga Ogah Junaid duk ya kori ƴan aikin gidan, saita jita shuru ba daɗi, ga yara na school shima idan ya fita yawonsa baya dawowa da wuri, gaba ɗaya zaman kaɗaici yayi mata yawa ga ayyukan gida sunyi mata yawa gaba ɗaya ta shiga damuwa sosai.... Akwana a tashi Uncle Artaff shima yana shirin barin Nigeria, zai koma can masarautar california da iyalansa, sunyi bankwana da kowa, anan ma Ayush ba ƙaramin shiga damuwa tayi ba ganin yanda kowa yaketa tafiya, Bayan tafiyar Uncle Artaff da wata guda shima Junaid ya tada nashi tafiyan zai koma california shima tareda su Ayushert, a hutun da aka bashi ma har ya ƙara kwanaki, Ayush ba ƙaramin farin ciki tayi ba jin wannan Albishir daga bakin mijinta, ga murnar zata je ta tarar da mommy tayi missing ɗinta sosai, amma abun mamaki duk yaran babu mai son tafiyar, saboda basa so subar school ɗinsu, ga waɗanda suka shaƙu sosai especially matan sunfi ƙawaye amma shi Areeph daman bashida wanda zaiyi missing ɗinsa sai iya Rapeekh domin shine kawai abokinsa, shima Rapeekh bason tafiyar Areeph yake yi ba, harda kukansa cewar Areeph zai bar Nigeria, sunyi shirinsu tsab, akan washe gari da sassafe zasu tafi airport domin har sun yanki Viza, Washe gari sun fito zasu shiga motar da zai kaisu airport kwatsam wani irin murɗa ya damƙi cikin Ayushert, bata san lokacin data fara jero addu'o'i ba, nan danan zazzaɓi mai zafin gaske ya rufe ta, ga hajijiya haka ta tafi luu zata faɗi Ogah Junaid yayi saurin tarota tareda faɗin "lafiya kuwa? meyake faruwa dake?..." kafin ta bashi amsa dasauri ta zame daga jikinsa ta nufi wajen fanfo anan ta tsuguna tana kwarara amai ba ƙaƙƙautawa, zuwa gabanta yayi ya tsaya yana kallonta yace "kodai mu fasa tafiyar nan yau naga bakida lafiya koh?..." girgiza kai tayi tace "ba komai zamu iya tafiya..." matsowa dab da ita yayi ya soma taɓa jikinta ji yayi kamar garwashi tsabar zafin da jikinta ya ɗau, lokaci guda ta fita hayyacinta ido sunyi zuru-zuru, shima girgiza kai yayi yace "gaskiya mu haƙura da tafiyar nan, idan kin samu sauƙi inyaso sai mu tafi koh?...". Nan danan saiga hawaye kwance a fuskarta ita sam bataso a haƙura da tafiyar tasa ranta sosai a tafiyar, tace "ina zumuɗi naje naga mommy dan Allah My kar kace bazamu tafi ba a yau, wallahi bana jin ciwon jikina..." yace "shikenam toh tinda kince haka, saiki wanke bakinki kizo mu tafi kar jirgin mu ya tashi .." a hanzarce ta wanke bakinta suka koma wajen mota, yaran kuma suna ciki sai wasan su suke ta sha yayin da shi kuma Areeph yake riƙe da wayarsa sai game yaketa yi, Ogah Junaid ko kaɗan bai kawo komai a ransa ba na dalilin aman Ayush, ya ɗauka cewa rashin lafiya ne na halin rayuwa yau da kullum, baiyi tunanin akwai ciki a jikinta ba saboda a yanda ta sanar masa shine tace "bata son haihuwa yanzu saita huta, kuma wai taje tayi Allurar planning na tsawon shekara huɗu..." Kuma tayi lissafi ne da cewar a yanzu yaranta sunada shekara huɗu a duniya idan ta ƙara shekara huɗu kuma sunada shekara takwas alokacin ne zatayi ƙoƙarin yi musu ƙani ko ƙanwa, saidai kuma data je yin Allurar planning sai akayi mistake maimakon ayi na yanda takeso 4 years sai akayi rashin sa'a sukayi mata na Three months kuma tin kafin Ogah Junaid ya dawo taje akayi mata, saidai kuma shi ba'a son ransa tayi planning ba, kawai ya ƙyaleta ne a haka.... A yanzu ko ita kanta bata san tanada cikin ba, saboda yana yin planning saida ya ɗauke mata jini kwatata daga baya ta dawo tana gani, kumadu ya ƙara ɗage mata haka yake mata shiyasa bazata san tanada pregnant ba, gashi har na tsawon wata biyu..... Haka suka shige mota sai airport anan suka shiga jirginsu, Haka su Areeph da Angel da Amrish suka rinƙa tsalle suna murna cewar yau zasu shiga jirgi wai basu taɓa shiga ba, Ogah Junaid sam baiji daɗin hakan ba, yaso ace yanda suke da kuɗin nan ace yaransa sun saba shiga jirgi, gashi yanzu yanda suketa tsalle kamar wasu baƙauyawa, son samu ace duk ƙarshen wata ana fita dasu yawon buɗe ido ƙasashe daban daban, amma laifin kansa yake gani da baiyi ƙoƙarin yin haka ba, ko ita Ayush ya kamata ace ta saba shiga jirgi amma itama yanzu ne karo na farko.... Bayan isar su ƙasar california a Babban Birnin Masarautar ƙasar suka sauƙa, Ayush gani tayi kamar ba masarautar ba duk an chancanza ko ina, suna daga cikin mota bayan sun sauƙa a airport daga cikin masarauta sarki Raamud ya tura driver akan yaje ya ɗauko su, gani sukayi an buɗe babban gate kai tsaye motar ta shige ciki, ga wasu manya-manyan Bodyguards a jere fuskokinsu kamar mutuwa ba alamar dariya, Areeph yana leƙensu ta window tareda cewa. "Daddy ina ganin waɗannan a Film, sune masu harbi da bindiga awajen yaƙi...." Murmushi kawai Junaid yayi jin yanda yaran suketa mita akan Bodyguards, bayan sunyi gaba sosai suka ƙara tarar da wani gate kuma du, nan ma buɗe musu akayi kumadu wasu ɗirka-ɗirkan baƙaƙen Amurkawa aka ajiye a jere saboda tsaro ga wasu manya-manyan karnuka da suke yawo a compound ɗin gidan, daga nan ne sai babban ƙaton cikin fada yanda manya-manyan baƙi suke zama domin tattaunawa da mai martaba sarki Raamud wato fadar sarki kenam, anan kuma kujerarsa take na zinare, anan suka sauƙa part ɗin sarki Raamud kenam kafin su wuce part ɗinsu, Karnukan nan har sun kewaye motar suna huci duk da sun san motar gidan ne amma so suke suga mutanen cikin, suna fitowa Ayush ta ƙanƙame Junaid da ƙarfi jikinta har kakkarwa yake ba ƙaramin tsoron kare take ba, ko a can Nigeria mah bata fitowa waje saboda karnuka har yaran suka saba, suma yaran fitowa sukayi duk da basa tsoron kare amma waɗannan karnukan sun razana su, saboda su kalarsu daban yake na turawa ga gashi tumuzu guda ajikinsu, suma karnukan ganin Ogah Junaid yasa duk suka kama gabansu saboda daman shine ya watsar dasu a cikin gidan, karnukansa ne, Haka suka shiga cikin babban falon su Mommy, ƴan aiki kawai suka tarar sunata aikace-aikacen su, duk zama sukayi akan kujeru Ayush kam bazata iya zama ba haka tasa akayi mata kwatancen yanda ɗakin mommy yake, da gudu take taka matakala har ta isa part ɗin mommy tana zuwa tasa hannu ta buɗe ƙofar ɗakin da fara'a akan fuskarta, abunda ta tarar ne yasa tayi go slow awajen, ido a zazzare take kallon mommy tana bawa yaro nono ga kuma ɗaya a kwance saman gado, Mommy kallon Ayush tayi tana dariya daman tasan dole abun zai bata mamaki, domin shima Uncle Artaff daya zo ya tarar da jarirai abun ba ƙaramin mamaki ya bashi ba, Mommy tace. "shugo mana Ayusher...". cike da tambayoyi a bakinta ta ƙarasa shugowa tana faɗin mommy mezan gani haka daman kin haihu ne shine baki sanar mana ba haba Mommy ..." Ayush tana ƙarasa maganar saiga Ogah Junaid shima ya shugo da sallama a bakinsa da Sarki Raamud yana riƙe da hannun Amrish da Angel, shima Junaid tsayawa yayi kamar wanda aka dakatar dashi, cikin rashin fahimta yace "Mom wadannan yaran waye? aina kika samo su, karfa ki cemun yaran wasu kika karɓa kina shayar dasu?..." Mommy tace "toh idan ba yaran wasu ba shin yaran wa kakeso nace maka?..." Gira a haɗe yace "yaran wasu mana, saboda ke dai nasan a yanzu bazaki haihu ba.." Ayush tace "Yaya Junaid wallahi mommy haihuwa tayi gashi tana shayar dasu..." Junaid hararar ta yayi sannan yace "kar ki gaya mun maganar shirme mana, nasan halin Mom yanzu haka ɗaukosu tayi a gidan marayu..." Ayush ta kuma cewa "toh tayaya ruwan Nono zai zo mata alhalin ba haihuwa tayi ba..." A ƙaiƙaice ya daka mata tsawa da cewa "yimun shuru, haihuwar lafiya..." Mommy dai kai a sunkuye ta kasa cewa komai ga yaro yanda yaketa shan breast, Sarki Raamud ne ya dafa kafaɗarsa yana cewa "Junaidd look at me, seriously Mom ɗinka ta haifi twins, kamata yayi kayi murna duk da nasan rashin sanar muku ne yasa ka shiga konkonto abun zaiyi matuƙar baka mamaki...." Kafin sarki Raamud ya rufe baki Junaid ya katse shi da cewa "Da kuma bani haushi ba, haba tayaya zanyi murna tsofe-tsofe daku kuna haihuwa, ku dubi ƙananun jarirai fah wai ku kuka haifesu wallahi abun yaban kunya, ina laifin Ni na haifesu, yanzu idan naje gurin Aiki mezance wa Abokai na da sauran yarana sojoji ina matsayin General nace Mamana ta haihu kenam? Impossible ku cigaba da ɓoye kuliyoyinku har su girma don nima babu a wanda zan gayawa, ai dole ku ƙi sanar mana kunya ce ta isheku, tayaya zaku ƙira kuce kun haihu daman ga jikokin ku...." yana kaiwa nan ya juya zai fita kawai kunnuwansa suka soma jin kukan ɗayan jaririya dake kwance akan gado alamar ta tashi daga bacci ne, Ayush tace "Mommy kawo wannan na hannunki na riƙe shi saiki shayar da wancan .." haka kuwa akayi mommy ta ɗauki ta kan gadon itama tasa mata Nono a baki, Junaid juyowa yayi yana kallonta da jariran jinjina kai yayi yace "Hmmm!!!..." ba tareda ya kuma cewa komai ba haka ya buɗe ɗakin ya fice, Sarki Raamud girgiza kai yayi yana murmushi domin sai yanzu ya tabbatar da cewa har yanzu akwai sauran ƙuruciya ajikin Junaid... Ayush ta kalli sarki Raamud tace "Abba Gaskiya banji daɗin rashin sanar mana da kuka yi..." Yace "sorry Ɓingel bazata mukaso muku daman, sai kunzo ku tarar da ƙannenku..." Mommy tasa baki da cewa "ƙannenku kuma kuliyoyinku...". Ayush kwashewa tayi da dariya sai yanzu ma abun yake bata dariya da maganganun Junaid, Shima sarki Raamud dariya yayi yana faɗin "Allah ya shiryi Junaid..." ya ƙarasa maganar tareda ficewa shima, Ayush ta kalli mommy tace "mommy kiyi haƙuri da maganganun Yaya Junaid..." Mommy tace "cabb haba Daughter kema dai kinsan nafi kowa sanin halin Junaid, wallahi ko kaɗan banji ciwon abunda ya faɗa ba, daman ai ya saba irin haka akan mai zan damu kuma, banda iya shege irinsa inda ace nayi Aure da wuri ai da yanzu ƙannensa sun girma, amma yana nan shi kaɗai kamar shaiɗan ba ƙanne ba yayu, ki rabu dashi kawai..." Ayush tace "gaskiya kam, ai Mommy naga baki tsufa ba, babu wanda zai ce ke kika haifi Yaya Junaid saidai wanda ya sani...." Mommy tace "daman ai shi ya tsufar dani, haba shekarunsa ma duka-duka 35 ne dai, ke kuma 25 yanzu daman ya baki shekara goma, tinda lokacin da Mamanki tabar gidan mu kina jaririya lokacin shekaransa goma, Babansa kuma yabar duniya..." Ayush tace "Ahhh mommy 35 ai ya girma shima ya kusan tsufa..." Mommy tace. "haba Ayusher lokacin danasa aka ɗaura Aurenku shekaransa 30 dai, yanzu kuma shekaranku biyar dayin Aure..." . jinjina kai Ayush tayi da murmushi a fuskarta, ta kalli jaririn hannunta tace "Mommy ya sunansu?.." Mommy tana riƙe da macen tace "wannan macece anyiwa Mamanki mai suna amma inkiya sunanta Ummul khair, Shi kuma na hannunki mai sunan Uncle Artaff ne yaci inkiya Abul-Ameen...." Ayush tinda mommy ta ambaci cewa anyiwa Umanta mai suna bakinta yake washe tsabar farin ciki, tace "wow Mommy naji daɗi sosai, Amma ni Ummy zan rinƙa cewa saboda Ummulkhair sunan yamun tsayi bazan iya faɗi ba..." Mommy dariya tayi tana cewa "kaii Daughter saikace ba ƴar gari ba har ki gagara faɗin sunan Ummulkhairy?..." gaba ɗaya dariya suke suna hirarsu abun burgewa kowa yana riƙe da jariri ɗaya..... Su kuma Amriish da Angel suna part ɗin sarki Raamud sai wasa yake tayi dasu, Areeph kuma yabi Daddynsa sunyi can part ɗinsu... Har dare Ayush tana tareda mommy anan suka ci abinci sukayi komai, daga baya Driver ya ɗaukesu a mota ita da yaranta biyu motar ta miƙe hanyar cikin masarautar, Ayush kalle kalle take tana mamakin irin girman masarautar nan, ga ya tsaru sosai saida suka isa bakin wani ƙaton gate tukun motar ta tsaya aka buɗe motar ta shige, nan ma Bodyguards ne suke gadin part ɗin, nan ne part ɗin su Ogah Junaid.. Part ɗin Uncle Artaff kuma sai an karya ƙwana tukun ɓangare ta dama kafin aje part ɗinsa shima akwai gate... Ayush tana shiga babban falonsu ta tarar komai tsab tsab ko tsinke babu an gyara ko ina, sai ƙamshin turare gaba ɗaya part ɗin yake, bata tarar da kowa ba haka ta soma taka dogon Beni ta nufi wani part wanda bata ma san inane ba kawai dai ta miƙa ne amma tana tunanin bedroom ne, amma kuma Benin ya kasu kashi biyu ne akwai ta ɓangaren dama da kuma hagun saita rasa ina ɗaya zata nufa, ga Amrish da Angel suma suna bin bayanta, Angel tace "Mommy wai ina zamuje karfa mu ɓata, mu jira Daddy acan ƙasan kujerun nan.." ta nuna ƙasan falo, Amrish tace "mommy mu fara shiga nan" ta nuna ɓangaren Dama, haka kuwa akayi suna buɗe ɗakin sukaga wani fankacecen gado dasu wardrobe da mirror da drowowi ga ƙofar toilet ta ciki har da ƙaramin table a tsakiyar ɗakin a yayin da kujeru suke kewaye dashi, ɗakin ba ƙaramin kyau yayi ba, Angel tace "wow Mommy ɗakin kwanciyar waye?..." Amrish tace "ke ɗakin kwanan mommy da Daddy ne kinsan tare suke kwana a gado ɗaya..." Angel tace "eh kuwa amma to mu ina ɗakin mu?..." Murmushi Ayush tayi tana jinsu tace "ɗakina daban na Daddynku daban wannan ɗaki nane muje na kaiku ɗakin Daddynku ..." Anan suka fita sai suka nufi Beni ta ɓangaren hagun anan ne suka tarar da wani ɗaki suna shiga suka tarar da wani ƙaramin falo ɗan ƙwaƙwass ga kujeru a jere da ƙaramin glass table a tsakiyar ɗakin, har da plasman a manne ajikin bango, kana taka ɗakin carpet yake nutsewa da ƙafarka sai kaji wani irin naushi kamar Audiga, ga wani irin sanyin A.C mai daɗin gaske, gurin yayi shuru sai ƙarar agogon ɗakin kake ji ƙitt! ƙitt!! ƙittt!!! ga wasu arnakun labulaye kalar carpet duk an zagaye jikin bango dasu, ta gefe guda kuma a jikin bango makeken photon Ogah Junaid ne yana sanye da Kayan Sojoji na nan ƙasar california yana manne da tambarin ƙarin girma na zamowa General, Angel ce ta zaro ido tareda cewa "Laaa Mommy ɗakin Daddy nane ga can ƙatoton photonsa..." Amriish tace "toh ai banga Gadon kwanciya ba kuma banga toilet ba dasu wardrobe da mirror..." Ayush ce tayi saurin rufe musu baki tareda faɗin "kuyi shuru naji motsi..." Duk sukayi tsittt, a hankali Ayush take taka carpet saboda ji take kamar zata nutse ciki tana bin hanyar da take jin motsi, buɗe labule tayi taga wani ƙofa kuma du tasa hannu ta murɗa take ƙofar ta buɗu tana shiga ta tarar da Ogah Junaid shi da Areeph suna kwance kan wani katafaren gado, tsayawa tayi ta kama kunkumi tana kallonsu, shi kuwa Junaid ya kara waya a kunne sai murmushi yaketa zabgawa alamun waya yake yi, Areeph kuma yanata gefensa tinin bacci ya ɗauke shi... Angel tace "wallahi room ɗin Daddy yafi na mommy kyau sosai..." Amriish tace "ehh mana ai na Daddy falo da bedroom ne, Allah yasa muma ɗakin mu irin wannan ne..." Angel ta kalli Ayush tace "mommy Daddy ya miki wayo ya baki ɗaki ɗaya na ƙwanciya shi kuma ɗaki biyu ya ɗauka falo da bedroom....." Ogah Junaid ne yayi musu alamar suyi shuru da yatsansa saboda karsu tashi Areeph yana bacci..." Ayush ganin bashida niyar gama waya kuma alama da mace yake waya yasa ta harareshi rai a ɓace taja hannun yaran suka fita, kai tsaye falo suka nufa, daga nan ne suka nufi wani part dake ƙasin beni anan ɗakin yaran yake, Angel da Amrish ɗakinsu ɗaya amma kowa gadon kwanciyarsa daban an ware musu, ga komai da komai acikin ɗakin har da computers na yara akan wani table dake gefe da kujeru biyu da mirror websites da wardrobe ɗinsu, ga toilet a gefen room, suma ɗakin nasun ba ƙaramin tsaruwa yayi ba, daga nan suka nufin ɗakin dake can gefe dasu ɗakin Areeph kenam suna shiga sukaga ɗakinsa yafi nasu tsaruwa komai nashi ɗan ƙwakwass, Akwai kuma ɗakin wasan yara daban an tanadar da kayan wasu irin su dokin roba manya-manyan wanda zasu iya hawa, da kekuna na yara har dasu motoci na roba wanda daga ɗan shekara ɗaya zuwa goma zasu iya shiga su tuƙa, komai da komai akwai su.... Ga kitchen ga store ga abubuwa daban daban babu abunda zaka nema ka rasa... ★★★★★ A kwana a tashi rayuwa tana tafiya yanda ya kamata, Ogah Junaid yanzu ya fara sauƙowa da fushinsa akan su Mommy haihuwar da sukayi, kullum indai zaije gurin aiki saiya bi ta part ɗin su yayi gaisuwa tareda kwasar Albarkarsu kafin ya wuce tin safe idan ya fita baya dawowa Sai Dare misalin ƙarfe 10, ga sojojinsa har gida suke rako shi da motoci, Yara kuma har an sakasu a wani private school na manya-manyan ƴaƴan masu kuɗi, a makarantar nan kuwa babu Yaren da yaro bazai koya ba, ko wani term ana biya musu kuɗin school fees duk yaro ɗaya dubu ɗari biyu su uku gaba ɗaya dubu ɗari shida (600,000) duk wata uku👌 Yaran Mommy kuwa Masha Allah, tufarkallah yanzu watansu takwas a duniya sun girma sun zama ɓuka-ɓuka kamar kajin agric, kyawawa dasu.. Ayush kuma tin daga lokacin da cikinta ya soma girma anan ta fara shiga tashin hankali da damuwa, abunda ta shirya ba haka taso gani ba, tayi mamakin ganin ciki a jikinta bayan tayi planning kuma, Babu yanda ta iya haka ta barshi amma ba haka taso ba, Shi kuwa Ogah Junaid yayi farin cikin ganin haka sosai saboda shi daman ba'a son ransa taje tayi Allura ba, yayi mata dariya sosai, sun tsara yawan yaranda zasu haifa guda biyar yanzu ga uku sauran biyu... Mommy kuma daman ta rufe haihuwa daga waɗannan twins... Ayush ciki ya girma sosai idan yara suka tafi school shima Ogah Junaid ya tafi gurin aiki wucewa take part ɗin mommy taje ta zauna wata rana kuma taje part ɗin Uncle Artaff, Ƙarfe 3 yara suke dawowa daga school kullum Driver zai kaisu ya kuma ɗauko su, ta ɓangaren Arabic kuma wani babban malami ne yake zuwa koya musu a gida duk wata ana biyansa albashi mai tsokar gaske, Karatun Alkur'ani sunyi nisa sosai kuma duk ajere suke tafiya dake yaran akwai ƙwaƙwalwa... ★★★★ Return to Nigeria Maimoon An samu ƙaruwa ƴa mace, su Rapeekh anyi ƙanwa Suma ta ɓangaren su komai Alhamdulillah 🙏, Itama Lailah tana nan da ciki ya fito sosai... Return to Jidda Hafzat dai ana nan anata cin Amarci har yanzu, babu wani motsin ciki sun tsara cewa sai sunyi shekara uku suna cin Amarci kafin su haihu, Babu yanda basu zagaya ba cin Amarci ƙasashen waje, sunje Saudiyya, sunje ƙasar India da Egypt da London da China dasu Canada da Cameroon sunje aikin Hajji, Umrah, Sunjejje california ma kaiwa su Mommy ziyara da Ayushert, Hafzat tayi kyau sosai dake tana samun kulawa yanda ya kamata ga duk ƴan uwan mijinta suna ƙaunarta basa son ganin laifinta, Akwana a tashi iyayenta ma sun zama shahararrun masu kuɗi a garin Kano dake Nigeria ata sanadiyar Hafzat, Itama Hafzat tana godewa Allah kuma akoda yaushe tana yiwa Ayushert addu'a fatan Alkhairi saboda ata sanadiyar ta take wannan matsayin, badan ita ba da har yanzu wata ƙila tana prison..... Ayush tana waya da mutanen Nigeria sosai taji labarin Doctor Hasheem da matarsa Maimoon sun jejje Hajji tana dawowa ta haifi ɗiya mace, Itama Lailah a amarcin ta mijinta ya kaita Makkah, Itama mommy anan sarki Raamud ya biya mata Makkah dake mommy duk shekara sai taje Hajj, A kwana biyun nan Ayush ko kula Ogah Junaid batayi tana fushi dashi saboda kowa yana kai matarsa Umrah da Makkah amma bai taɓa kaita ba ko sau ɗaya, banda nan california da suka dawo bai taɓa fita ƙasar waje da ita ba, Har kwatance take masa da Hafzat yanda mijinta Judan yake fita da ita ƙasashen waje amma ita yaƙi kaita kuma Junaid yafi su kuɗi sosai nesa ba kusa ba, Saboda ƙorafinta yasa shi cewa yayi mata Alƙawari idan ta haihu zai kaita Makkah da sauran ƙasashen waje, Amma taƙi yadda tace "ita nan duniya kafin ta haihu take son zuwa Makkah inyaso idan ta haihu saita je sauran kasashen Turai, haka ta dage akan saita je makkah saboda karta mutu kafin ta haihu ko a wajen haihuwa... Ogah Junaid babu yanda ya iya haka yaje ya biya mata kujerar Makkah, har baza'a karɓeta ba saboda cikinta amma dake akwaj kuɗaɗen haka aka yadda akan zataje kuma yanada magoyan baya sosai.... Bayan Sati biyu Ayush angama shirya komai akan zata tafi Makkah, farin ciki kamar bazata mutu ba, taso taje da Ogah Junaid amma sam yaƙi zuwa sai haɗata yayi da Uncle Artaff akan zasu tafi tare saboda ana buƙatar muharraminta, Shikenam su Ayush an tafi Makkah.... *LITTAFI YAZO ƘARSHE BAZAMU TSAYA BADA LONG STORY BA, AGURGUJE ZASU SAMU MU KAMMALA, YANZU DAI DAGA NEXT PAGE SHIKENAM MUN GAMA...* 𝑡𝑦𝑝𝑖𝑛𝑔✍️ 𝗠𝗔𝗧𝗔𝗥 𝗗𝗔𝗠𝗨𝗦𝗔 the wife of a tiger🐅🐅🐅🐅 𝙼𝚊𝚕𝚕𝚊𝚔𝚒𝚗 𝙰𝚜𝚖𝚎𝚎𝚝𝚊𝚑 ✍️✍️ 𝙿𝚊𝚒𝚍 𝚋𝚘𝚘𝚔 𝚌𝚊𝚕𝚕 𝚘𝚛 𝚠𝚑𝚊𝚝𝚜𝙰𝚙𝚙 09065443871 *💫💫{{N W A}}💫💫* Book two C̶h̶a̶p̶t̶e̶r̶ 96 to 100 The End~End~End ★★ Of★★ The wife of a tiger Bayan wata guda da tafiyar Ayushert aikin Hajj, Ogah Junaid yana zaune a Babban office ɗin shi sai faman danne danne yake a cikin computer sai ji yayi wayarsa tana ring-ging, bai tsaya duba wayar ba sai ya cigaba da aikin gabansa domin ya saba irin haka sai a ƙirashi sau nawa amma bai ɗaga ba kuma yana kusa da wayar, bayan ƙiran ya katse sai kuma aka turo da message, anan ne yakai hannunsa kan wayar domin duba saƙon da aka turo masa, lokaci guda ya miƙe tsaye a razane yana faɗin "what .." Ƙirjinsa ne ya hau bugun uku uku ido a zazzare, daƙer ya iya haɗiyar yawu wanda ya tokare masa maƙogaro, ganin text ɗin ba karamin razana shi yayi ba, {Sorry your wife....} abunda aka rubuta kenam, ya gagara gane mai hakan yake nufi, dasauri yabi number da akaita ƙira amma abun mamaki lokaci guda akayi switch up, jiki ba ƙwari ya fice daga office ɗin, yana fita a gaggauce ya shige motarsa kai tsaye gida ya miƙa domin tabbatar da abunda ke faruwa da matarsa, ko zasu iya sanin komai... Mommy tana dinning tana shirya kayan abinci a sarki Raamud, wannan aikin ba na masu aiki bane aikinta ne, saida ta gama tsab zata haura upstairs ta nufi ɗakinsa kwatsam taji ana ƙwallah mata ƙira tin kafin a shugo falon, mommy ba ƙaramin tsorita tayi ba tace "innalillahi wa inna ilaihi raju'un, Allah yasa dai lafiya ..". dasauri ta sauƙo falo daiden lokacin da Junaid ya shugo hankali a tashe ya nufeta tareda faɗin "meya faru da Yushert?..." saida gabanta ya yanke a tsorace tace "wani abu ya faru da ita ne?..." Nuna mata message da aka turo masa yayi mommy ta karɓa tana dubawa lokaci guda ta sauƙe ajiyar zuciya tana hararar sa tareda cewa. "wallahi saika kashe mai rai, haba wannan wani irin tayar da hankali ne haka, Ni nayi tunanin wani abu ya faru ne ashe abunda aka rubuta kenam..." Junaid yana kallon mommy yace "sorry your wife?...! Abunda aka rubuta kenam toh amma me hakan yake nufi? shin meya faru da ita? kuma ba ita ta turo wannan message ba still nabi number but switch up...." sai a yanzu itama mommy ta shiga yin nazari tace " wait bari na ƙira number Sameeha naji meke faruwa ne saboda Ayushert a wajenta ta sauƙa..." tana shirin ƙira saiga ƙiran Uncle Artaff mommy tace "yawwa ga Uncle ɗinku ma ya ƙira.." ta ɗauki ƙiran tareda sallama, mommy tace "yadai naji muryarka sanyi² meke faruwa?..." Junaid eyes ɗinsa akan mommy kansa har wani juyawa yake, saiji yayi mommy tana faɗin "Alhamdulillah Masha Allah mai aka samu?.." daga ɓangarensa ya bata amsa da cewa "Namiji...". Mommy tace "toh amma ita Ayush tana lafiya koh?.." Uncle Artaff bai bata amsa ba ya katse wayar.. cike da mamaki tace "ha'a lafiya kuwa".. Junaid jin ance Namiji ne har yaji sanyi a ransa, ya ɗaga hannu sama yana godewa Allah cike da farin ciki, ya kalli mommy yace "amma wanda ya turo saƙonnan ba ƙaramin tsorata Ni yayi ba, me makon yasa congrats amma wai sorry, Sorry for what?..." Mommy tace "toh yanzun ya za'ayi?..." Junaid yace "me kuwa za'ayi illa a ɗauko mun matata da jariri a dawo mun dasu gida..." Mommy tace "haka ya kamata ayi, kawai zance wa Uncle Artaff su dawo gida kawai ko kuma Ni naje na dawo da ita..." Junaid yace "gaskiya Mom gobe da sassafe jirgin Makka zai tashi yakamata kije da kanki, yaranki kuma tinda sun fara wayo kuma ga masu aikin ki kawai ki barsu...." tace "ehh daman barinsu zanyi, yanzu dai bari naje na samu Abbanku na sanar masa..." Junaid ya amsa tareda ficewa daga part ɗin gaba ɗaya, kai tsaye part ɗinsu ya nufa... Bayan shigar Mommy room ɗin Sarki Raamud tarar dashi tayi akan sallaya bayan ya idar da Sallah ya kifa kansa akan gwiwowinsa, itama zama tayi akan sallayar dab dashi ta ambaci sunansa cool voice. "My King.." Ɗagowa yayi da rinanan idanuwansa waɗanda suka kaɗa sukayi jaa tsabar kukan da yasha, mommy a tsorace taja baya cikin tashin hankali take faɗin "Subhanallahi Mai martaba mai zan gani haka, kuka fah kake yi? Na juma ban ganka acikin wannan halin ba dan ALLAH ka sanar mun..." Jinjina kai yayi sannan yace "yanzu na gama yin waya da Artaff..." Mommy cike da mamaki tace "nima nayi waya dashi yake sanar mun cewa Ayushert ta haifi ɗa Namiji..." Girgiza kai sarki Raamud ya shiga yi yace "Ɓingel ta haifi Jaririnta kuma yana nan cikin ƙoshin lafiya amma sai dai ita ta rasa tata Rayuwar...". wani irin razana mommy tayi tareda ja da baya tana faɗin "innalillahi wa inna ilaihi raju'un⁴..." haka ta rinƙa nanatawa lokaci guda ta kifa kanta aƙasin carpet ta fashe da matsanancin kuka jiki na kakkarwa, Sarki Raamud jiki ba ƙwari haka yake rarrashinta shima yana zubda ƙwallah, daƙer yake furta "kiyi haƙuri kulli nafsin za'ikatul maut, duk mai rai mamaci ne...". Mommy kuka take ba bakin magana, a wannan ranar haka ta wuni tana wannan kukan... Washe gari mommy da Sarki Raamud sun shirya akan zasu je makkah, amma sun kasa sanar wa Junaid halin da ake ciki, shi a tunaninsa zasu je ne su taho da ita da Jaririnta... Bayan kwana biyu da tafiyarsu, Ogah Junaid yana zaune a babban falonsa yana kallon tv ga Amrish kwance saman cinyarsa ta damu sosai da rashin ganin mommyn ta, kullum saita tambayi yaushe zata dawo, kullum tana cikin kuka wai ita akaita gurin mommynta daƙer Junaid yake rarrashinta domin Amrish tanada rarraunar zuciya kamar Ayush, abu kaɗan take saka abu aranta, ita kuwa little Angel tana can tanata wasanta bata damu ba, tayi kewar mahaifiyarta amma akoda yaushe tanasa ran zata dawo, shi kuma Areeph koda yaushe yana cikin dube duben littafinsa na school, ko kuma yaita danne² computer sam bai damu da tafiyar Mommynsa ba saboda yasan zata dawo... Ogah Junaid yana zaune yasan yau ne su Mommy zasu dawo, saboda hakane yasa tinda suka tafi bai fita yaje gurin aiki ba saboda yaran, Ji yayi an buɗe gate mota ta shugo, yana jin parking mota yasan su ne suka dawo da murmushi akan fuskarsa ya ɗago da Amrish yana faɗin "Mamana tashi maza ga mommynki ta dawo..". a ruɗe ta tashi tana cewa "Mommy ta dawo ina take? kafin su nufi bakin ƙofa saiga su Mommy sun shugo da sallama a bakinsu tana ɗauke da Jariri a hannunta, sai sarki Raamud yana biye da ita da kuma Uncle Artaff su uku, Junaid kallonsu yake ganin ba Annuri a fuskokinsu, idon mommy a kumbure yanda tasha kuka, haka suka shugo gaba ɗayansu suka zazzauna akan kujera shima Junaid zama yayi ya kasa cewa komai, ita kuwa Amrish da gudu taje ƙiran sauran ƴan uwanta cewa Mommynsu ta dawo, Ogah Junaid murya na kakkarwa yace "ina take?..." Mommy sunkuyar da kai tayi ƙasi tana sharar hawaye, Uncle Artaff ne yayi ƙarfin halin cewa "Junaid kayi haƙuri akan abunda zamu ce maka, inaso ka kwantar da hankalinka kayi imani da ƙaddara mai kyau ko akasin haka, mu sani cewa duk rintsi duk wuya wata rana zamu bar duniya ko yau ko gobe kai ko yanzu ma idan Allah yaso zai karɓi rayukan mu..." Cikin rashin fahimta Junaid yake bin Uncle Artaff da kallo yace "Please uncle duk nasan da wannan nidai buƙatata a sanar mun a inda Yushert ta tsaya, na ƙosa dana ganta kuma ƴaƴanta suma sun damu sosai..." Mommy ce ta taso daga yanda take zaune ta zo gurinsa tareda miƙa masa Jariri tace "ganan yaronta nan ita bata samu damar zuwa ba..." yatsina fuska yayi tareda faɗin "ban gane bazata samu damar zuwa ba, shin meya faru da Yushert ne kuke ƙoƙarin ɓoye mun?..." Sarki Raamud kam babu bakin magana sai hawaye domin yayi babban rashi a rayuwarsa, Ɓingel Abar ƙaunarsa kuma farin cikinsa.... Uncle Artaff yayi ajiyar zuciya sannan yace "kayi haƙuri Ayshert Allah yayi mata rasuwa..." Junaid jin kansa yake kamar a sama yake ga wani irin hajijiyan da yake ɗibansa Lokaci guda, a ruɗe yace "whattt...". yana riƙe da Jariri a hannu badan a zaune yake ba babu abunda zai hana hajijiya ya ɗebe shi, lips ɗinsa ne yake kokarin motsa shi amma ya kasa furta komai, lokaci guda idanuwansa suka rine sai hawayen dake gangaro masa, a hankali yakai idonsa kan yaron yana ƙareshi da kallo, girgiza kai ya soma yi tareda faɗin "i can't believe, Yushert bazata mutu ta barni ba, inaji ajikina Ni zan rigata mutuwa, zanje na ɗauko matata tinda kun kasa tafo mun da ita..." a gigice ya miƙawa mommy yaron dake hannunsa yana sambatu ya tashi zai nufi waje, Sarki Raamud yayi saurin riƙo shi yana faɗin "kayi haƙuri mana Junaid, ka sani fah kowa ma zai mutu kuma lokacinta ne yayi, ka godewa Allah ta hanyar Haihuwa ta mutu, tana buƙatar addu'ar mu dan Allah ka kwantar da hankalinka...." Junaid idonsa akan sarki Raamud daƙer yake motsi da bakinsa yace "Abbah da gaske Yushert ta mutu?..." Jinjina masa kai kawai yayi yana zubda ƙwallah, cikin ƙanƙanin lokaci numfashinsa ya ɗage luuuu yayi baya zai faɗi sarki Raamud yayi saurin taro shi yana faɗin "innalillahi wa inna ilaihi raju'un Junaid! Junaid!! Junaid!!!..." haka ya kiɗime yana ƙiran sunansa amma ko motsi Junaid babu, Mommy tana zaune kawai ta fashe da kuka, Uncle Artaff ne shima ya miƙe suka ɗago shi kai tsaye upstairs suka haura dashi yanda zai kai su room ɗinsa... Mommy ɗagowar da zatayi idanuwanta suka sauƙa akan Triplets suna tsaye suna kallon duk abubuwan da ke faruwa, Amrish ganin yanda Daddynsu ya faɗi aka ɗauke shi yasa jikinta ya soma ɓari yana kakkarwa kamar mejin sanyi, ta tsaya cak ta kasa motsawa a yayinda Angel da Areeph suka nufo gurin Mommy suna faɗin "Mamy meya samu Daddyn mu?..." dake sunan da suke ƙiranta dashi kenam, Mommy tace "babu komai ta ƙarisa maganar tareda goge hawayen fuskarta..." Areeph yace "Mamy kina kuka kuma kina ce mana babu, shin meya samu Daddyn mu kuma ina Mommyn mu take?..." Itama Angel tace "wannan Jaririn waye?..." Mommy tace "Jaririn Mommynku ne ta haihu...". Angel ta kuma cewa "toh tana ina Mommyn namun?..." Mommy ta kasa basu amsa kwatsam idonta ya sauƙa akan Amrish wacce take tsaye guri ɗaya sai fitar da numfashi take sama-sama, a tsorace mommy ta tashi ta nufi wajenta tareda faɗin "takwara meya faru ne? dan Allah ki temake mu kar ciwonki ya tashi please, ki kwantar da hankalinki kinji koh..." Haka take rarrashin ta cikin kulawa domin ita daman Amrish batada cikakkiyar lafiya an haifeta da ciwon zuciya amma ba'a ankara ba sai bayan ta soma girma, zuwa yanzu dai sau biyu ciwon yake tashi, shiyasa akafi lallaɓata kuma tanada raunin zuciya bata juran damuwa, fargaban mommy a yanzu shine kar ciwon ya tashi a halinda take ciki yanzu... Amrish ba abunda take faɗi illa "Mommy! Daddy!! Mommy!!! Daddy!!!!...". Ido yayi zuru-zuru. Mommy tasa hannu ta rungumeta tana rarrashinta ta ɗayan ɓangaren kuma tana riƙe da Jariri, Can saiga su Uncle Artaff sun sauƙo yace "Suma yayi amma yanzu ya farfaɗo yana buƙatar hutu domin jikinsa yahau temporary...". Sarki Raamud yasa hannu ya ɗauki Amrish zasu tafi da su can part ɗinsu... Bayan Kwana biyu Ogah Junaid yana nan a cikin Damuwa na rashin matarsa uwar ƴaƴansa kullum sai mommy taje parts ɗinsa tayi masa girki daƙer take rarrashinsa akan yaci amma duk da hakan baifi yaci 2 spoon ba shikenam, gaba ɗaya ya lalace duk ya rame cikin kwana biyu, ba bacci ba cin abinci sosai kullum acikin damuwa, mommy har ta rasa yanda zatayi dashi, A ranar ciwon zuciyan Amrish ya tashi a part ɗin mommy acikin tana motsawa har ta daina motsi kwata-kwata, numfashi ya ɗage cakk ga jinin dake fita a bakinta gaba ɗaya Mommy ba ƙaramin razana tayi ba, duk sun saddaƙar da cewa Amrish itama ta mutu, domin babu alamar da zai nuna cewa tana a raye, haka sauran ƴan uwan natan suka fara kuka, itakam Angel ihu take tana ambatan sunan Amrish, shi kuwa Areeph shima faɗuwa yayi ganin ƴar uwarsa ta mutu, duk ana cikin wannan halin Amrish ta mutu shima Areeph ya faɗi amma an kasa sanar wa Ogah Junaid dake can part ɗinsa saboda ana gudun tayar masa da hankali, yanzu ma ba'a cikin hayyacinsa yake ba, Mommy ta kasa aiwatar da komai duk jiki ya mace sai kukan da take tayi, Sarki Raamud ne ya ɗauki wayarsa ya ƙira Uncle Artaff akan yazo, kafin nan kuwa acikin ma'aikatan gidan an samu wacce tayi gudu taje har part ɗin Ogah Junaid tana zuwa ta haura saman Upstairs taje tana bubbuga room ɗinsa, Junaid yana kan sallayarsa yanda ya idar da Sallah yana kan addu'o'i kunnuwansa suke jiyo masa bugun ƙofa kamar daga sama, kafin ya buɗe baki yayi magana kwatsam yaji an turo ƙofar da ƙarfi wata mata ƴar dattijuwa ta shugo ta durƙusa a gabansa tana haki numfashi sama-sama yanda tasha guda, Junaid kallonta yake hankali a tashe domin yasan ba lafiya ba, fuskarsa har yayi fiyau, idanuwansa kuma suna nan a dishe basu koma normal ba, Haka ya jira saida matar da daidaita numfashinta sannan ta soma magana tana faɗin "Yallaɓai Amrisha ciwon zuciyarta ya tashi ta rasu, shima yaron Areeph ya faɗi suna can..." Ogah Junaid idanuwansa ya zazzaro waje kamar zasu faɗo ƙasi, lokaci guda hawaye suka bayyano masa akan eyes ko ƙibtawa bayayi idonsa akan matar, tana gama iddasa saƙonta ta tashi ta fice abunta, haka jikinsa yake kakkarwa ya miƙe a razane hajijiya yana ɗibarsa haka ya nufi hanyar fita, Da gudu yake taka matakalar beni yana saƙƙowa ƙafarsa ta zame haka ya faɗo yana gangarowa daga kan Benin har zuwa ƙasi, nan danan goshinsa ya fashe sai jini, ƙafarsa ta gurɗe Allah ya temaka bai karya wuyansa ba, tsabar yasa yaran acikin ransa haka yayi ƙarfin halin tashi yana jan ƙafa daƙer ya fice daga falon, yana jin jiri amma haka yake daurewa, cikin sa'a ya samu driver part ɗinsa cikin hanzari ya shige mota Driver ya miƙe dashi part ɗin su mommy, yana zuwa ya tarar da mommy zaune ƙasan carpet tana rungume da Amrish sai kuka take tayi shi kuma Sarki Raamud ya ɗauki Areeph a saman kafaɗarsa, ganin Junaid a wani irin yanayi yasa gaban Sarki ya yanke tareda faɗin "subhanallahi Junaid meya sameka haka, dubi fuskarka duk ya wanke da Jini..." Mommy najin haka ta ɗago dasauri tana kallonsa still yana tafe yana ɗingishi! a ruɗe Junaid yayo gurin mommy tareda durƙusawa yakai hannu ya ɗago da Amrish yana bubbugan fuskarta tareda ambatar sunanta "Mamana! Mamana!! Please wakeup Mamana don't leave your Dad please....". ya rungumeta tareda fashewa da matsanancin kuka, ya miƙe tsaye da ita ya ɗorata saman kafaɗarsa ya nufi gurin Sarki Raamud yaje ya karɓo Areeph wanda shima yana nan a sume ba motsi duk ya ɗaukesu su biyun ya fice waje, yana zuwa ya sakasu a mota shima ya shiga kai tsaye cikin masarautar suka ƙara shigewa suka nufi hospital ɗin Narasimha, daga baya su Mommy suma suka biyo bayansu da nasu motar gaba ɗaya sun mance da hospital ɗin Narasimha tsabar tashin hankali da suka tsinci kansu shiyasa tin da basu kai yaran nan ba... Suna zuwa Narasimha ya farfaɗo da Areeph daman suma yayi, Amrish kuwa saida akayi aiki sosai akanta, domin saida akayiwa heart ɗinta aiki sannan akayi nasarar ceton rayuwarta, shima Ogah Junaid anyi masa treat na ciwon da yaji sannan an haɗa masa da maganin rage damuwa dana saka bacci domin rabonsa dayin bacci yau kwana uku kenam bai rintsa ba, Ogah Junaid da yaransa sai da sukayi sati guda a wajen Narasimha domin yaƙi barinsu su tafi har saida Amriish ta fara samun sauƙi, Idan suna tare da Daddynsu hankalinsu yafi kwanciya especially Amrish yanzu da take ganin Daddynta ta daina damuwa sosai, kullum sai mommy ta aiko musu da abinci, yanzu kuwa Ogah Junaid ya daina fita Aiki kwata-kwata tin lokacin da aka sanar masa rasuwar Ayushert ɗinsa, Bayan an sallame su da wata guda Ogah Junaid yana kwance a saman gadonsa ga yaran suma suna kusa dashi a jere duk suna bacci, yanzu duk tare yake kwana dasu, su huɗu akan gado dashi kansa Junaid sai Areeph da Angel da Amrish, Amriish ko kaɗan bata son motsawa ajikin Daddynta hakan yasa ta fara kwana a room ɗinsa itama Angel ganin haka yasa tace bazata iya kwana ita kaɗai a ɗakinsu ba itama ta fara kwana da Daddynta, shima Areeph ganin duk a ɗakin Daddynsu suke yasa shima ya dawo ɗakin, kullum kuwa sai mommy ta kawo musu ƙaninsu Jariri har ya fara wayo, dake madara mai kyau da tsada ake bashi, yaron ya samu sunan sarki Raamud inkiya kuma (KHUBAYR) wannan inkiyar Ayushert ce tin kafin ta haihu tabar wasiyya akan a sanya masa sunan... Daga Nigeria sun samu labarin mutuwar Ayush kowa ba ƙaramin girgiza yayi ba dajin labarin, especially Doctor Hasheem yafi kowa shiga damuwa sosai, duk sun shirya akan zasu zo ƙasar california yin ta'aziyya, Doctor Hasheem da matarsa Maimoon da yaransu biyu sai Lailah da mijinta Doctor Mansur da yarinyar ta mace, da Daddyn Maimoon da mamanta duk sun zo, Mommy ba ƙaramin farin ciki tayi ba ganin yanda duk suka haɗa kayuwansu suka zo musu ta'aziyya, Sunyiwa Ogah Junaid shima duk ya canza ya zamo kamar Maraya babu kuzari ajikinsa, saida suka ƙwana kafin suka dawo Nigeria... Daga baya Hafzat itama da mijinta suka je, tinda hafzat take bata taɓa yin kukan da tasha a lokacinda aka sanar mata rasuwar Ayushert ba, har sukazo kuka takeyi gaba ɗaya ta fita hayyacinta, bata bar masarauta ba sai da tayi wata guda kafin saboda bataso tabar Triplets, ba ƙaramin tausayinsu tayi ba na rashin uwa tin suna yara.... ★★★★★★ *AFTER 2 YEARS....* Har zuwa wannan shekarar Ogah Junaid bai koma Aikin soja ba, a matsayinsa na General duk aikin da zaiyi saidai yayi daga gida, idan ana bukatar yasa hannu a takarda saidai a kawo masa gida yasa hannu duk wasu ayyukansa a gida yake yinsu, yanzu shine yake kula da yaransa, suma yaran sun ƙi school a duk lokacin da aka kaisu makaranta sai sun dawo da jinya a jikinsu tsabar ɗankwara har yanzu basu fitar da wannan damuwar na rashin mahaifiyarsu ba, akoda yaushe suna tsammanin dawowarta, ga khubayr ya girma ba tareda mahaifiyarsa ba yanzu yanada shekara biyu a duniya, yana samun kulawa sosai agurin ƴan uwansa, tsabar shaƙuwar da sukayi baya son yin nisa dasu don ko gurin mommy yanzu baya zuwa.. Ogah Junaid yana kwance ya ɗora Khubayr a saman ƙirjinsa sai bacci yaketa sha, ta gefen hannunsa kuma Amriish ce take kwance akan Damtsensa itama sai bacci taketa sha, ta ɓangaren ɗayan hannunsa ta dama kuma Angel ce itama tana kwance akan hannunsa tana shan bacci, Areeph kuma yana can gefen gado shima baccin yake yi, Banda shi Ogan wanda idonsa biyu yana kallon ceilling fuskar Ayush kawai yake gani, har yanzu yana cikin wannan damuwar na kewar Matarsa, yana cikin wannan tunanin yaji an turo ƙofar ɗakin Mommy ce ta shugo da sallama a bakinta tana murmushi saboda kusan kullum a haka take samun su, da kular abinci a hannunta, ta ajiye akan table tana faɗin "toh Sarkin thinking kai baka bacci koh?..." Murmushi yayi sannan yace "Hmmm! Mommy kenam .." ta zauna a bakin gadon itama tana bin yaran da kallo tace "ka sabar wa yaran nan zama guri ɗaya, basa wasa sannan basa zuwa makaranta why?..." Yace "Mom it's not my fault, har yanzu akwai damuwar rashin mahaifiyarsu acikin zukatansu, na rasa yanda zanyi na cire musu, idan na matsa a kusa dasu gani sukeyi kamar nima zan tafi na barsu ne kamar yanda suke tunanin Mommynsu ta tafi ta barsu..." Mommy tace "a hankali zakana cire musu abun a ransu, yanzu tsawon shekara biyu amma har yanzu basu daina kewar nan ba? waɗannan wasu irin yara ne haka, yanzu suke da shekara shida fah, gashi har sun koyawa ƙaramin ƙaninsu zaman kewar, yakamata suje su haɗu dasu Ummulkhairy da Abul suna yin wasa tare kuma su rinƙa zuwa school, kar ka sakalta su da haka .." Ajiyar zuciya Junaid yayi yace "toh yazanyi especially Mamana duk ta fisu ɗankwara ganinta koda yaushe ajikina ne yasa suma suka biye mata, ina tsoron tashin ciwonta, inda ace Yushert tana nan da duk hakan bata faru ba, amma zanyi iya ƙoƙari na naga sunje school sannan duk zasu koma ɗakunan su da kwana...." Mommy tace "toh kai kuma fah? Kaima ai kamar yaran haka kake kaƙi komawa gurin aikinka..." Yace "saboda yaran ne yasa bana zuwa..." Mommy ta ɗanyi shuru kaɗan daga baya tace "Amm daman inaso zanyi magana dakai..." Ogah Junaid cike da mamaki yace "ina jinki Mommy...' Tace "daman maganar akan Aurenka ne, bai kamata ace kana zaune haka ba mata ba, idan kayi Auren suma yaran zasu fi jin daɗin kasancewa cikin nishaɗi..." Junaid haka yake jin kalaman mommy a baibai cikin rashin fahimta yace "Aure kuma? da wa?..." Mommy tace "mun zauna mun tattauna da Baffanunka akwai wacce zamu haɗaka da ita, Balarabiya ce ƴar ƙasar Makkah, tanada kyakykyawar zuciya, kuma zata riƙe maka yara tamkar mahaifiyarsu, idan har kaji halayenta da tarbiyarta zakaso kasancewa tareda ita a matsayin matarka, yaranka zasu ji daɗin kasancewa da ita domin ita ɗin uwar ƴaƴa ce tanada son yara sosai da sosai, ka yadda dani my son kasan bazan zaɓa maka abunda zai cutar dakai ba..." Ogah Junaid jinjina kai yayi shi ya rigada ya tsara cewa bazaiyi Aure ba, zai tsaya ne ya kula da yaransa.... Yana cikin wannan tunanin yaji mommy ta katse shi da cewa "na roƙe ka my son ka amince dan Allah, ina neman alfarmanka..." Kallon mommy yayi tareda haɗiyar yawu yace "shikenam Mom, babu abunda zaki roƙeni akan nayi shi banyi ba, domin kin wuce haka acikin zuciyata! duk abunda kika tsara dai dai ne saboda haka na Amince, indai kin yadda da tarbiyarta nima na yadda..." Murmushi mommy tayi tana hamdala cike da farin ciki tace "Nagode sosai Yarona, Allah Ubangiji ya maka Albarka, Allah ya ƙara maka haƙuri da juriya, Allah ya ƙara buɗa maka ƙofofin Alkhairi..." Junaid ba ƙaramin jin daɗi yayi da waɗannan addu'o'in mommy ba, shima yayj murmushi yace "Nagode Mom, Allah yabar mun ke..." ta Amsa da Ameen sannan ta sanar masa cewa "Gobe insha Allahu su Baffanunka zasu je su ɗauro maka Aure acan ƙasar Makkah..." Zaro ido Junaid yayi sannan yace. "Mom da sauri haka?..." Tace "kai baka saniba har an gama komai yanzu Aure ne ya rage, inada yaƙini zaka amince shiyasa tinda ban sanar maka ba..." Murmushi kawai yayi ba tareda yace komai ba, Mommy ta fice a ɗakin cike da murna... Bayan fitar ta kwantar da kansa yayi akan pillow kansa na kallon ceilling shi yasan irin damuwar da yake ciki na rashin Ayush...... Washe Gari su Uncle Artaff da Sarki Raamud sun shirya tsab zasu tafi Makkah, Ga jirgi na jiransu haka suka tafi, Junaid yana tareda yaransa bai ma san sun tafi ba saboda bai saka abun aransa ba, mommy haka tasa ƴan aiki suka gyaggyara ko ina na gidan, part ɗin Ogah Junaid an gyara wuri yayi kyau sosai, A wannan lokacin a falo suke zaune suna kallo Angel tace "Daddy ya naga duk an gyara gidan, waye zai zo?.." Junaid yayi murmushi sannan yace "Aunty za'a kawo muku gidan..." Angel tace "Aunty kuma aina?..." Yace "Aunty za'a kawo muku wacce zatana kula da ku.." Angel kamar zatayi kuka tace "kenam Mommyn mu bazata dawo ba har abada?...". Junaid jiki ba ƙwari haka yake kaɗa mata kai. Amriish tace "mommy ta gudu ta bar mu, ta guje mu, bata son mu, nima yanzu na daina damuwa da ita inaso a kawo mana wata Aunty wacce zatana kula damu, kuma zata zauna a matsayin Mommyn mu..." Ogah Junaid yana kallon Amriish cikin tausayawa yace "Mommyn ku bata guje ku ba..." Kafin ya ƙarasa maganar Areeph ya katse shi da cewa "mommy fah mutuwa tayi.." Junaid cike da mamaki yake bin Areeph da kallo daƙer yake motsi da lips ɗinsa waran cewa "waya gaya maka cewa Mommynku ta mutu?..." Areeph yace "na daɗe dajin labarin nan a wajen su Mamy....." kafin ya rufe bakinsa Amrish ta cabki wuyansa tana kuka tana faɗin "wallahi mommy bata mutu ba, ƙarya kake yi mommyna bata mutu baa.." nan suka fara kokuwa tsakanin Areeph da Amrish Ogah Junaid ganin Areeph ya ware hannunsa zai zabga mata mari yasa yayi saurin riƙe masa hannu tareda rabasu kowa yaja shi gefe, gaba ɗaya ya rasa mai zaice mAh, Ita kuwa Angel fashewa tayi da kuka jin ance Mommynsu ta mutu,... Daƙer ya rarrashe su sannan yaja su suka nufi bedroom..... Su Sarki Raamud basu tashi dawowa ba sai washe gari suka tafo da Amarya tareda wasu matan waɗanda suka yo rakiya, ana kawo Amarya aka wuce da ita part ɗin Angonta wanda yasha tsaruwa sai ƙamshin turare ne yake faman tashi, Shima Ogah Junaid yasha Gizner abunsa ba ƙaramin kyau yayi ba, sannan Angel da Amrish suma an haɗesu da dogwayen riguna na kanti masu kyan gaske da tsada kayansu iri ɗaya, shima Areeph da Khubayr sunsha Gizner irin na Daddynsu, sun sha kyau sosai kamar ƴan indiyawa kodama asalin ƴan India ne... Misalin ƙarfe 10 na dare Ogah Junaid yana zaune a falo shida Yara suna kallon Film saiga Mommy ta shugo da flask a hannunta tana ganin Junaid ta tsaya tana kallonsa gira a haɗe, Junaid yana ganin mommy a haka yayi murmushi yace "Mom what's wrong?..." Tace "haba My Son yanzu fisabilillah hakan ya dace kenam!?.." Yace "me kuma nayi?..." Tace "meyasa kabar Amarya ita kaɗai acan room ɗinka baka je ka ganota ba?..." Murmushi yayi sannan yace "Mom zanje so nake sai yaran sunyi bacci ." Tace "a'ah basu ga Auntyn nasun ba zasuyi bacci?..." Angel tace "Daddy nikam zanje naga Auntyn namun..." Itama Amrish tace "nima zanje naga Auntyn mu wacce zata zamo Mommyn mu.." Mommy tana tsaye sai Dariya take tayi tace "toh shikenam kuje room ɗin Daddynku tana can, kuje kuce mata ta fito kuci Abinci...". Suka amsa da toh suna tsalle suka haura upstairs... Shikam Areeph ƙin zuwa yayi yana tsaye sai faman haɗe rai yake tayi, shi daman baiyi murnar Auren ba, mommy ce ta fahimci Areeph yana cikin ɓacin rai tace "Angona lafiya kuwa meyasa bazaka je gurin Aunty ba?...". ya kawar da kai gefe tareda faɗin. "Ni indai ba mommy nah bace bana sonta, kuma naji kunce mommyna ta mutu..." Gaba ɗaya jikinsu ne yayi sanyi daga mommy har Ogah Junaid, duk suka kasa cewa komai, ga Khubayr a cinyar Daddynsa sai tsotsar babbar yatsarsa yake idonsa akan TV dake yaro ne bai san me ake tattaunawa akai ba, kuma shi baiyo wayon yayunsa ba, saboda shi har yanzu Khubayr bai iya magana ba, su kuma triplets tin suna yashi suka fara magana... Suna cikin wannan halin saiga Amriish ta sauƙo down tana kuka Mommy tace "takwara meya faru ne?..." Tana kuka tana faɗin "wannan Auntyn namun taƙi buɗe fuskarta mu ganta kuma taƙi zuwa muci abinci..." Mommy tace "a'ah kuyi mata uzuri kunya take ji..." Mommy ta kalli Junaid sannan tace "tashi muje na rakaka ɗakin Amaryarka inyaso saiku ci abinci gaba ɗaya acan..." Junaid bai Musa ba haka ya tashi tareda ɗora Khubayr saman kafaɗarsa sannan ya riƙo hannun Areeph suka fara taka upstairs, itama mommy tana biye dasu a baya tana riƙe da flask ɗin ferfesun chicken duk suka haura, suna shiga ɗakin suka tarar da Angel a kusa da ita tanata kokarin leƙa fuskar Amarya ta cikin mayafinta, mommy tace "Amarya bakya laifi ƴaƴanki suna son ganin fuskar Auntynsu ki temaka su ganki mana..." Amriish itama kusa da ita taje tana cewa "muna so ki zama Mommyn mu, kinga Mommyn mu ta guje mu, ta gudu ta barmu bata son mu...." Itama Angel tace "bamu san laifin mai mukayi mata ba, har ciwon zuciyan Amrish yaita tashi sauran kaɗan ta mutu amma taƙi dawowa..." Amriish fashewa tayi da kuka tana cewa "bata tausayin mu, ciwo na yaita tashi ina aman jini, ƙirjina yaita ciwo sosai...". Itama Angel kuka take ta riƙo hannun Amrish tana cewa "kiyi haƙuri Amrisha kar ciwonki ya ƙara tashi kinga mommy ba zuwa zatai ba, kawai muma mu manta da ita...." Amriish tace "Ni daman babu ruwana da mommy, yanzu bana sonta tinda ga Auntyn mu kawai sai ta zama Mommyn mu koh?...". ta ƙarasa maganar tana gayawa Angel, Ogah Junaid yana ɗauke da Khubayr lokaci guda ya tsinci kansa a wani irin yanayi, tinin hawaye suka wanke masa fuska, jin yanda yara suke ganin laifin mahaifiyarsu wacce ta daɗe da barin duniya... Mommy itama jikinta ba ƙaramin sanyi yayi ba, haka hawaye yake gangaro mata ba ƙaramin tausayi yaran suka bata ba... Itama Amarya ta kasa buɗe fuskarta acikin mayafi duk tana jin maganganun da yaran suke yi, sun bata tausayi sosai tana daga cikin mayafin amma kuka take yi sosai... Areeph shima matsowa kusa dasu yayi yace "na gaya muku Mommyn mu mutuwa tayi..." Amriish tayi saurin katse shi da cewa "a'ah ba mutuwa tayi ba guduwa tayi ta bar mu..." Angel itama cewa tayi "meyasa ba'a sanar mana ta mutu ba, kuma banga mutane sun taru a gidan ba, ta haifi ƙanin mu ta aiko mana shi amma ita taƙi dawowa saboda bata son mu...." Amriish fashewa tayi da matsanancin kuka tana faɗin "ku daina mun maganar Mommy ciwo na zai tashi, na fara jin ƙirjina ciwooo...." Itama Angel fashewa tayi da kuka tana cewa "kiyi haƙuri Amrisha bana son ciwonki ya tashiii..." Shima Areeph ɗin kuka ya soma yi ganin yanda ƴan uwansa suke kuka kuma sam baya son ganin ciwon Amriish ya tashi... Ogah Junaid shima kukan yake yi yakasa dakatar da yaran da maganganun da suke yi akan mahaifiyarsu jin Amrish tana maganar ciwonta zai tashi ba ƙaramin tsorita yayi ba, haka zuciyarsa take bugun uku uku, nan danan ya miƙawa mommy Khubayr dake hannunsa yana ƙoƙarin nufan yanda suke kar Amrish ta faɗi... Mommy abun mamaki yake bata ganin yaran tsawon shekara biyu amma sun kasa cire abu a ransu... Junaid ganin Amarya tayi saurin durƙusa gwiwowinta a ƙasi duk ta rungumi yaran su uku a jikinta tareda fashewa da matsanancin kuka mai ratsa zukata, kuka take sosai still fuskarta na cikin mayafi tana rungume dasu, Yaran ganin yanda ta rungumesu tana kuka yasa suka dakatar da yin kukan suna kallonta, Abun yayi matuƙar ɗaure wa Junaid kai shin tausayinsu ne yasa take kuka haka ko kuma mai? Kunnuwansa ne suke jiyo masa wani irin sauti wanda zaiyi wuya ya manta kalar sautin? wato kukan da yake jin Amaryarsa take yi, haka ya matso kusa dasu hannu na kakkarwa ya janye mayafin kan Amaryar, Cikin firgici da tsoro haka Junaid yaja baya a razane da ƙarfi yake furta "Innalillahi wa inna ilaihi raju'un...". sauran kaɗan ya faɗi ƙasi yayi saurin dafe jikin gini ido a zazzare yana kallon Amaryar... Ɗagowa tayi tana bin yaran da kallo cikin kuka har eyes ɗinta sunyi jaa tsabar kukan data sha, Areeph da Angel da Amrish zaro ido sukayi waje cike da fargaba duk suka haɗa baki wajen cewa " *MOMMY*.." tana kuka tareda faɗin "ku gafarce ni yarana, dan Allah ku yafe mun! Nasan banyi muku daidai ba amma inasonku har cikin zuciyata, ina ƙaunar ku..." Angel cikin kuka tace "Mommy kin dawo gare mu?...". ta rungumeta tareda cewa "na dawo yarana kuna nan a cikin zuciyataa..." Amriish itama kukan take tace "mommy kika sa ciwona yaita tashi sauran kaɗan na mutu...". Cikin yanayin kuka ta jawo Amriish jikinta ta rungumesu sosai kamar zata mayarsu cikinta, Areeph shi kam babu bakin magana yana rungume da Mommynsa shima yana kuka yace "mommy akace kin mutu ashe ƙarya akeyi baki mutu ba..." Tace "yarona ban mutu ba, gani na dawo gareku bazan taɓa yada ku ba har abada..." duk suna rungume da juna sunata kuka babu mai rarrashin kowa daga uwar har ƴaƴan... Ogah Junaid kam a tsaye ya ƙafe baki na kakkarwa cikin ƙinƙina yace "Yushertttt....." wani irin sanyi taji a zuciyarta jin an ambaci sunan da ta juma ba'a ƙirata dashi ba... Idonta a lumshe a hankali take buɗe su har eyes ɗinta suka sauƙa akan Junaid wanda shima idonsa akanta yake, A hankali ta ɗago da yaran daga jikinta duk ta sumbace su akan goshi sannan ta tashi ta nufi gurin da Junaid yake tsaye, wani irin kuka ne ya kuɓuce mata tayi saurin shigewa jikinsa ta rungume shi sosai tana kuka, A ruɗe ya soma yin magana yana cewa "shin mafarki nake yi ko kuwa abunda idona yake gane mun gaskiya ne? Dan Allah idan mafarki nakeyi kada ku tashe Ni har sai na kammala ganawa da Yushert ɗina..." Muryar mommy yaji yo tana cewa "ba mafarki bane gaskiya ne, tabbas Yushert ɗinka kake gani a zahirance ba mutuwa tayi ba tana nan da ranta..." Junaid ɗago da ita yayi suna fuskantar juna yace "tayaya hakan zata faru tsawon shekara biyu uwa tabar ƴaƴanta, mata tabar mijinta...". Ayush kasa cewa komai tayi sai hawayen dake gangaro mata, Mommy tace "Ba laifinta bane nasan bazata taɓa barin ƴaƴanta har tsawon wannan lokacin ba, sannan tana ji tana gani bazata iya haifar jariri ta barshi atafi mata dashi har tsawon wannan lokacin bata ƙara ganinsa ba, Waɗannan tambayoyin da zakayi inaso ka adana su zuwa gobe da safe duk zakaji abunda ya faru, yanzu dai kabar uwa ta gana da ƴaƴanta kaima miji ka gana da matarka...." Ta kalli Ayush tace "ganan jaririn ki har ya isoki girma..." Ayush tana kuka tasa hannu ta karɓi yaronta a hannun mommy tana faɗin "Khubayr my son, nayi kewarka tin haihuwarka kullum tunanina akan wannan yaron da kuma sauran ƴaƴana da mijina duk nayi kewarsu...." Khubayr har yayi bacci yatsa a baki sai tsotsa yake kamar wanda ya samu Nono, duk da yanzu ya wuce shan Nono two years now, Mommy ficewa tayi daga ɗakin ta basu guri, around 11:30Pm yanzu... A wannan daren Ayushert da Ogah Junaid kwana sukayi basu yi bacci ba a yayinda sauran ƴaƴan suka jeru duk sunyi bacci gasu akan gado gaba ɗayansu, sunyi kewar junansu sosai..... Washe Gari kowa na gidan ya hallaru a babban fadar masarauta, ga sarki ga Mommy, uncle Artaff shi da iyalansa sai Ogah Junaid da Ayush ga yaranta duk sun mamaye ta... Uncle Artaff ne ya kalli Junaid sannan yace "kayi haƙuri Junaid mun san munyi maka laifi, mun ɓoye maka abunda baka sani ba, Ayshert ta shiga wani irin yanayi na ciwo wanda har anyi tsammanin ta mutu bayan ta haifi Jaririnta, har anyi mata wankan gawa an suturtata acikin likkafani za'a bisineta akaga ashe ba mutuwa tayi ba, saidai ta haɗu da ciwon hauka da kuma mantau hakan yasa muka tafo da iya Jaririnta, saboda babu halin shayar dashi domin bata san a yanda take Bama, sakamakon Jinn da suka raɓeta na cikin masarauta, sihirin dake jikinta na cewar babu wani Jinni dazai raɓeta ya karye hakan yasa tarin manyan Aljanu suka bibiyeta kuma niyarsu su rabata da Duniya saboda Aljanun da mahaifinta ya ƙoƙƙona su ta hanyar tsafi sune suka bibiyi Ayushert domin ɗaukar fansa, sun juyar mata da ƙwaƙwalwa, sun sa ta mance da ƴaƴanta, sun sa ta mance da mijinta, inda ace mun kawota nan yaranta bazasu samu nutsuwa ba sannan idon Aljanun zasu karkata zuwa kan yaran hakan yasa muka barta acan sannan muka sanar maka cewa ta mutu, Malaman garin Makkah sun taya mu da addu'a sosai, da maganinnuwa na Musulunci saida aka dage da roƙon Allah tukun Allah ya bata sauƙi amma taci azaba bana wasa ba, kaima kanka Junaid bazakaso kaga Ayushert a wannan yanayin ba, domin ta koma tamkar Aljana, ason ransu in har basu kasheta ba toh kuwa zasu mayarta jinsinsu na Aljanu kuma zasu iya ɗauketa su mayar da ita duniyar su na Aljanu, a gaskiya ka godewa Allah sosai, Addu'a itace makamin mumini kuma itace ta ceci Ayusher daga hannun Azzaluman Aljiin, wannan tsawon shekara biyun duk ana fama ne dasu amma yanzu Alhamdulillah 🙏, yanzu babu wata matsala dazai ƙara afkuwa mana kumadu.... Sarki Raamud yana hawaye yace "haƙiƙa na ƙona ƴaƴan Aljanu ba adadi hakan yasa na nemawa Ɓingel sihiri wanda babu Aljanin dazai raɓeta sai gashi an wayi gari babu sihirin ashe kuma Aljanu sun ɗana mun tarko akan ɗiyata ....... Haka suka zauna sunata tattaunawa duk acikinsu babu wanda baiyi kuka ba, Da haka har kowa ya koma part ɗinsa... After one Month Ayushert taje ɓangaren swimming pool yawon shakatawa tana sanye da doguwar riga baƙa mai botula har ƙasi ta gaban rigar, tana tsaye a bakin ruwa ga sumar kanta a baje ya sauƙa har gadon bayanta, ita kaɗai sai murmushi take tayi kwatsam taji an dafa kafaɗarta a tsora ce ta waiwaya tana faɗin "innalillahi wa inna ilaihi raju'un....". daiden lokacin da ƙafarta ya zame tayi baya zata faɗa cikin ruwan a ruɗe shima yakai hannu zai riƙota tayi saurin cabko rigarsa suka faɗa cikin ruwan a tare, Saida suka nitse cikin ruwan lokaci guda suka ɗago da kayuwansu suna maida numfashi, Ayush turo baki tayi tana kallonsa cikin yanayin shagwaɓa tace "ka tsoratar dani over...". ya rungumeta tareda cewa "toh Sarkin tsoro...". Bugan ƙirjinsa tayi tana dariya nan suka fara wasa a cikin ruwan kowa yana watsawa kowa, suna cikin wannan yanayin shauƙin saiga triplets suma sunzo wajen har da Khubayr wanda yake binsu da gudu duk yanda suka je, Areeph yace "Daddy mommy me kukeyi acikin ruwan?..." Ogah Junaid yace "wanka muke yi mana..." Haka duk suka haɗa baki wajen cewa "muma zamuyi wankannn...." Yace "toh shikenam duk kuzo...". Duk suka cire kayan jikinsu daga su sai pant, shima Khubayr cire masa sukayi suna zuwa duk suka faffaɗa cikin ruwan, Khubayr kam Mommynsa ce ta ɗauke shi acikin ruwan saboda shi bai iya ruwa ba, ana ajiye shi zai nutse ciki, haka suka rinƙa wasa a cikin ruwan nan Iyaye da ƴaƴa duk ɗin su, Saida suka kammala suna daga cikin ruwan Ogah Junaid ya ɗauki Areeph akan wuyansa, sannan ya ɗara Jarumarsa wato little Angel akan kafaɗarsa, itama Amrish ya ɗauketa ata ɗayan hannun, Ayushert kuma tana ɗauke da Khubayr ta shige tsakiyar Ogah Junaid itama, *NI KUMA ASMEETAH WACCE NA KASANCE MAI ƊAUKARSU A PHOTO NA SAITA KAN CAMERA TA NAYI SHUTTTTT NA ƊAUKE SU A PHOTO.....* Alhamdulillah 🙏 Alhamdulillah 🙏 Alhamdulillah 🙏 ala kulli hali... Allah ina mai ƙara gode maka daka bani damar fara rubuta littafina mai suna Matar Damisa yanzu kuma ka bani aron kwanaki na gama littafina cikin ƙoshin lafiya, Ya Allah duk kuskuren da mukayi acikin littafin ina mai neman yafiyarka, Astagfirullah Allah ka bani ikon fara New book ɗin na cikin kwanakin nan🙏🙏 Masoyana Nagode sosai da Addu'o'inku 🙏 Allah Ubangiji ya haɗa kayuwan mu agidan Aljanna🙏🙏🙏