MASARAUTAR MU! Littafin SUMAYYAH ABDULKADIR takorikabara@gmail.com SADAUKARWA Ga Bilkisu Askira, (Billie Askira), Maiduguri, sabida gudummuwar ki yayin rubuta wannan littafi. JINJINA Har kullum jinjinar taku ce dukkan members na TAKORI'S ONLINE FORUM whtspp, littafin MASARAUTAR MU jinjina ne a gare ku, nagode da kauna da kwarin gwiwa, ni da ku hadin Allah ne. Allah ya bar mana zumunci har gidan aljannah. GARGADI Ban yarda a karanta wannan littafi a kowacce kafa ta sadarwa ba batare da iznina ba, tun daga radio, facebook, whtsp idan har ban yi izni ba, yin hakan karya doka ne kuma abin tuhuma ne daga lawyer na Barrister Sadiq Rufa'i Wali. SHIMFIDA Rana ta tasamma faduwa, misalin karfe biyar na yamma. Lahadi ce, wadda ta kasance ranar kasuwar kauyen. Tsanyawa, karamar hukuma ce a cikin birnin Kano. A dai-dai wannan lokacin kasuwar garin ta fara watsewa, kowa na kokarin komawa gida cikin iyalin sa domin lokacin magariba ta kawo kai. Malam Hashimu, daya daga cikin dattijan garin Tsanyawa, dattijo ne mai kamala dan kimanin shekaru sittin da biyar, ya baro kasuwar akan keken sa, wani tsohon keke wanda da kyar tayoyin sa ke juyawa sabida tsatsa da tsufa. A hankali yake tafe a gefen hanya kikiki-kikiki....bayan keken sa dauke da tsarabar kasuwa ta kayan miya (kayan gwari) wadanda yake sayarwa da tsarabar yalo, dafaffen rogo da rake dasu agwaluma cike taf a katuwar leda. Tun daga bayan darnin gidan sa ya ke jiyo tashin kukan diyar sa SA'ADE. Zuciyar sa ta tsinke...kamar koyaushe ya ji kukan yarinyar tasa. Ya kara gudun keken sa ya iso gida jikin sa yana rawa, da hanzari ya jinginar dashi a jikin jinka ba tare da ya bi ta kan ledar tsarabar sa ba, ya fada gidan da dan banzan sauri, babbar rigar sa tana harde shi saura kadan ya fadi, da kyar ya samu ya dafa katangar dakin sa ya shigo gidan kamar an jefo shi. Abinda ya zata shi ya gani, wato mai dakin sa ce Inna Laure ke jibgar Sa'ade, da wani murtukeken iccen darbejiya tun karfin ta, yarinyar tana ta ihu da neman taimako kamar kullum. Hannu ya mika ya daga yarinyar wadda ke kuka kamar ranta zai fita tana fadin..... "Baba ka cece ni Inna zata kashe ni....". Inna Laure ta yarda iccen tana masifa tana fadin. "Gobe ki sake dawo min da sauran gasara baki sayar ba, ki ga yadda zanyi da ke a gidan nan. Haka kawai ki dinga jaza min asara, ai ba uban naki ya bani jarin ba, in baza ki yi min talla ba, to ya dauke ki ya yi miki aure. Ba zan zauna ina ciyar daku ga banza ba, kartin banza kartin wofi da basu san komai ba sai ci da juyewa a masai, dole ki fita ki nemo min tunda kun zame min jaraba daga ke har sullutun uban naki da bai ko iya ciyar da gidan sa". Malam Hashimu bai ce komi ba, amma ba kalmar data fi bakanta mai rai cikin maganganun ta irin "sullutu", ya tada yarinyar ya kama hannun ta suka nufi dakin sa. Har zuwa lokacin Sa'ade kuka take yi jikin ta yayi birdin-birdin yana ta rawa. A gefen wata tsohuwar kujera kwalli daya da ke dakin mahaifin nata ta zauna, ta takure jikin ta tana sheshsheka hadi da hadiyar zuciya. Malam Hashimu ya ce "bar kukan ki gaya min kin ci abinci?" Sa'ade ta girgiza kai hawaye na sakko mata. "Baba tun kokon safe, ban kara cin komai ba". Tashi yayi ya koma inda ya jingine kekensa ya dauko kullin ledar da ya dawo da ita, ya dawo ya zauna a gaban 'yar tasa. Kwancewa yayi ya fiddo daurin awara mai zafi a cikin leda ya tura mata gaban ta ya ce "maza cinye". Sa'ade ta shiga tunkuda awara a bakinta hannu baka hannu kwarya, daidai lokacin aka bankado labulen dakin aka shigo. Laure tasa hannu ta dauke kullin awarar gabadaya tana fadin "eh lallai! Gata mugun abu, in baki dambu ki ci ki koshi, ki cewa ubanki ban baki abinci ba ko? To daga ke har shi kun yi kadan ku nuna min iyakata a gidan nan, idan bazaki ci abinda na dafa da kaina ba, sai dai ki kwana da yunwar ki". Ta fice kamar kububuwa tana maganganu da fadace-fadace kamar sabon kamu. Malam Hashimu ya sunkuyar da kai, Allah kadai ya san abinda ya ke tunani, zuwa can ya dago ya ce "Sa'ade!" Cike da haushin baban nata wanda ba ya iya tabuka komai a gidan sa, Laure ta gama raina shi sabida sanyin halin sa. Sa'ade ta daga kai ta sauke manyan idanun ta akan mahaifin ta. Ya ce "me yasa data baki dambun baki ci ba?" Ta bude baki cikin murya ta wanda ya ci kuka ya koshi ta ce "Baba ni bata bani ba, babu dambun data bani, bana gidan ma, tun safe ta dora min tallan gasara. Ni kuma sai na tafi makarantar su Hanne na tsaya a bakin taga ina jin yadda ake koya musu karatu, sai da aka tashe su na tafi tallan gasarar, kuma har yamma tayi ban sayar gabadaya ba, na dawo mata da saura shine take duka na". Girgiza kai yayi ya ce "ki yi ta hakuri kin ji Sa'ade? Watarana sai labari. Insha Allahu sai Laure ta amfana da ke watarana, ina raye ko bana raye kullum ina gaya mata wannan. Ni Allah bai dora min iya fada da masifa ba, bana son su, ban kuma iya su ba. Shi yasa na barta da halin ta. Ki cigaba da yi mata biyayya, ita din duk yadda take uwa ce a gare ki. Da dadi ba dadi ta rike ki har kika kawo munzalin da kike yau. Shi yasa nake kauda kai akan duk muzgunawar data ke miki kada ta ce don ba ita ta haife ki ba........". Sa'ade ta katse Baban ta da sauri da tambayar data dade tana cin ta a zuci. "To Baba ni wacece uwata? A ina take? Ka ce tana raye, amma meyasa ban taba ganin ta ba ko a hoto?" Fuskar Malam Hashimu nan da nan ta tattare ta koma kamar jikakken tsumma, ba ya son tuno ta.....ba ya son tuno duk abinda zai tuna masa da ita...... ta bar masa tabon da har abada bazai taba bacewa daga zuciyar sa ba! Ba kuma zai taba gayawa Sa'ade inda take ba har sai ita din ta nemeta da kanta, wanda ya san mawuyaci ne tayi hakan; a matsayin da take kai a yanzu, da kuma shi data gujewa. Da Sa'aden data haifa bada son ran ta ba! Ya riga yayi amanna da cewa....... ko bajima ko ba dade zata nemi Sa'ade, a lokacin da zai nuna mata shine ubanta duk talaucin sa. Mulkin ta bai yi isar da zai kwatar mata 'yar ta daga hannun sa ba. Idanun sa suka kada suka yi jazur da ya tuno kiyayyar uwar ta gare shi, mummunar kiyayyar da ko a hikaya bai taba jin irin ta ba, ba don komai ba sai don shi talaka ne? Idan yayi la'akari da inda take aure ta kuma yi zaman ta yanzu? Daga ita sai shi, sai Ubangijin ta suka san dalilin kiyayyar ta gare shi. Murya a sanyaye ya ce. "Ga Yalo da dafaffen rogo yi maza ki ci ki debi ruwa a randa ki sha, ni zan je na yi alwallah". Ya fada yana mai kaucewa kaifin manyan idon Sa'ade, wadanda a lokuta da dama suke firgita shi ya ganta ta rikide ta koma masa kamar BILKISU! Sa'ade bata dauke idanun nata daga kansa ba har ya bar dakin, sannan ta ci dafaffen rogon ta koshi, bayan ta ture yalon gefe, ba ra'ayin ta bane. Ta kora da ruwan randar baban dake gefe mai sanyi da gardi. Ta mike ta fito tana leken Inna Laure a madafi, da ta ga hankalin ta ya dauku ga tukin tuwon data ke yi sai ta kwashi takalmanta a hannu ta danna a guje ta fice daga gidan. Gida biyar ne a tsakanin gidan su da wanda ta shiga, ta maqe murya tana fadin "Hanne tana nan? Ta zo inji Iliyasu!" Hanne wadda ke alwala a gindin rijiya tayi murmushi ba tare da ta juyo ba ta ce "Sa'aden Baba, Sa'aden Hanne, Naziru na kira a dandali!". Suka kwashe da dariya a tare. Sannan Sa'ade ta shigo tana fadin "ai ban baki labari ba, jiya da ya zo waje na Inna Laure ta dage sai na fita, ina zuwa mun fara gaisawa ya saki wata tusa kamar mushen jaki, don wari ba shiri na gudu gida, gara mun dukan Inna akan tusar Naziru. Kuma lazim ne kullum ya zo sai ya yi ta. Ni me yayi min zafi da Naziru? Ga saurin tusa sannan ga shegen surutu". Hanne sai dariya take yi harda hawaye. "Inna Laure ke son sa sabida yana kawo mata dankalin da yake sayarwa kuma yana bata 'yar murtala idan ya zo". Innar Hanne ta fito daga bayan gida rike da buta da alama alwala zata yi, duk abinda suke fadi tana jin su, a ranta amincin su yana bata sha'awa, ta ce "Ho! Sa'aden Hanne, ba'a fita da manghariba fa, na hana ki amma bakya ji, zo ga abinci na ajiye miki na san ba ki ci ba" Sa'ade ta tsugunna ta gaida Innar Hanne, ta wuce madafi kanta tsaye don ta dauki abincin data ce ta dauka. Kusan kullum sai Innar Hanne ta ajiye mata abinci. Sai da suka yi sallah sannan suka ci abincin ita da Hanne a kwano guda, suna ci suna hirar samarin su suna kwasar dariya, Hanne ta roki Innar ta zata raka Sa'ade gida kada Inna Laure ta doke ta. Har dakin Inna Laure Hanne ta raka Sa'ade, wadda ke rabe-rabe a jikin bango irin na wanda ya san yayi laifi, da Hanne ta fita ji tayi kamar ta bita a guje. Hanne na bada baya Inna Laure ta shaqo Sa'ade ta makure ta a jikin bango ta ce. "Shine don kar ki kwashe min tuwo kika faki ido na kika tafi gantali ko? To kin yiwa kwanon tuwon ki, ko loma daya bazan baki ba, ki kwana da yunwar ki, 'yar banza mai mugun hali irin na uwar ta". Sa'ade dai bata tanka ba, don inda sabo ta saba ji a bakin Inna Laure uwartamai mugun hali ce. Kuma dai a koshe take, don haka bata damu ba data ce bazata ci tuwon dare ba. ****** Washegari ma da Inna Laure ta dora mata gasara maimakon tabi gida-gida kamar yadda ta ke yi sai ta karkata hanya ta tafi makarantar su Hanne, yau ma a bakin taga ta tsaya daidai saitin da Hanne ta ke farantin gasarar ta yasar da shi a gefe. Malamin yana cikin bada darasi ya hangota tana leke. Zagayowa yayi ba da sanin ta ba sai ganinsa tayi a bayan ta, ta zabura zata gudu ya tare hanya. "Shiga aji ki zauna, zan sa Dagaci ya yiwa baban ki magana, kullum ina ganin ki kina leken kawayen ki, wanda ke nuna kina sha'awar karatun da muke yi". Bakin Sa'ade ya ki rufuwa don dadi, sai dai ta sani Inna Laure bazata taba bari ba, shi kuwa Baba sai abinda tace sabida tsoron masifar ta. Hankalin ta ya dauku ga abinda ake koya musu A BA CA DA Ee FA GA HA.....! Sa'ade ta bude murya tafi kowa yi... abinda ya dauki hankalin malamin a kanta ya gane da gaske take son karatun. Don haka kamar yadda yayi alkawari har kasuwa ya bi Malam Hashimu bayan sun tashi, cikin nutsuwa ya neme shi ya bar Sa'ade ta dinga zuwa makaranta a daina dora mata talla. Malam Hashimu yayi shiru, daga bisani ya ce a sanyaye, "uwar rikon ta bata so, kada ka sa ni a tashin hankali ina zama na lafiya". Sa'ade data zo washegari malam yace tayi zamanta, ana tashi yaje ya gayawa Dagachin Tsanyawa, shi kuma ya tura aka kira masa Malam Hashimu da Laure, a gabanta ya ce yayi umarni ga Malam Hashimu ya saka 'yar sa a makaranta a daina dora mata talla lokacin zuwa makaranta, idan kuma sun ki to su tattara su bar Tsanyawa dama dukkan su ba haifaffun garin bane, gara Laure wadda ta zo da ita Tsanyawa daga kauyen Kiyawa 'yar asalin garin ce. Shi kuwa Malam Hashimu Dagaci ya ce har gobe bai san daga ina ya zo ba. Mafari kenan da Sa'ade ta samu 'yancin zuwa makarantar boko har da ta allo, wannan bai hana Laure cigaba da dora mata talla ba a duk lokacin da ta dawo. Tana aiki tana mita tana tsinewa Dagacin Tsanyawa. A wannan lokacin ne makerin budurci ya soma kera Sa'ade, ta fara kirgan dangi har da jinin al'ada a shekarun ta goma sha biyu kacal. Hanne ce ta koya mata kunzugu, da wankan sallah da tuni Innar ta ta koya mata don ta riga Sa'ade farawa. Manema suka yiwa Sa'ade Caaaa! Manya da yara. Kai ka ce wata budurwar kirki ce, bayan Naziru mai dankali harda dan Dagachi dake karatu a birni, da wani Alhaji Talle mai mata uku amma yana da sukuni sosai. Kyawun fuskar ta shine abinda ya ke fara jan hankalin maza a kanta, wani irin sassanyan kyau ne da ita na mutanen wani yanki daga BORNO da ake yiwa laqabi da shuwa-arab wanda ake rasa gane daga inda ta samo shi don kwata-kwata bata yi kama da mahaifin ta ba, wanda yake baki, tittirna, mai gajeren hanci. Mutane da yawa a garin na fadin Sa'ade ba 'yar sa bace, tsintota yayi, don babu wanda ya san shi da uwar ta, kawai an wayi gari ne an ganshi a garin tare da yarinyar 'yar shekaru uku yana rainon ta. Daga baya ya nemi auren Laure, ba bata lokaci aka bashi ba tareda binciken asalin sa ba don ta buwayi marikanta kuma ta rasa mijin aure duk fadin kauyen. A tsakankanin wannan lokacin ciwon da aka rasa gane kansa ya kama Malam Hashimu, tun yana yi a tsaitsaye har ya gagara fita kasuwa, kullum abu kara gaba yake yi, banda jike-jike ba abinda yake sha don Laure ta ce sisin kwabon ta ba zai yi ciwon kai ba wajen kai shi asibiti, ita ba haihuwa ba a barta da asara. Sa'ade ko makaranta daina zuwa tayi sabida jinyar baban ta, kullum ce mata yake ciwon sa ba na tashi bane, bai damu ba don ya mutu a wannan lokacin, ita Sa'ade ce damuwar sa. Wa zai rike masa ita? Ina za ta je idan bai tashi ba? Ya sani Laure ko a kafa aka daura mata Sa'ade sai ta kwance ta yar. Sabida tsanar data yi mata. Damuwa ta karu akan ciwon Malam Hashimu ta yi sanadin da ko idonsa baya iya budewa. Sa'ade na ji Laure na gayawa mutanen da ke zuwa duba shi wai ciwon daji ke damun sa. Baban Hanne shine ya tausayawa Sa'ade ganin halin da take ciki na fita hayyaci sabida ciwon Baban ta, duk da shima ba wani karfi gareshi ba haka ya kukkuta ya samo motar akori -kura ya tafi dashi asibiti a cikin Kano. Ba yadda Sa'ade bata yi ba zata bisu amma Malam Sale yace ta zauna a ranar zasu dawo. Har kwana uku basu dawo ba, a kwanakin nan uku Sa'ade ta gama karewa a tsaye, bata ci bata sha. A rana ta hudu kuwa tana gindin murhu tana hurawa Laure wutar tuwo taji ana fadin. "Ku shigo da shi daga ciki, a kawo tabarmi.......". Sai ihu da kururuwar Laure. Tana fadin "Malam ashe sa'i ya yi? Ashe rabuwar kenan?" Fitowar Sa'ade a guje daga madafi yayi dadidai da shimfide gawar da aka yi a tsakar gidan su. Da gudu ta karasa ta bude fuskar ta tabbatar Baban ta ne..... Ya rasu! Tafiya ta har abada wadda babu dawowa........ Ji kake yiff! Ta fada kan gawar a sume bata kara sanin inda kanta yake ba. ***** Ta farfado ne ta ganta a gidan su Hanne, Hanne na kuka Innarta na mata firfita. A lokacin ne abinda ya faru ya dawo cikin kwanyar ta. Ta rushe da kuka tana fadin "Hanne da gaske ne Babana ya rasu?" Innar Hanne ta rungumota jikin ta tana ta lallashinta tare da bata kalamai masu dadi. Sai da aka kwana bakwai Sa'ade bata daina kuka ba, kulawa da kauna ta duniya babu wadda iyayen Hanne basu gwada mata ba don dai su samu ta kwantar da hankalin ta ta karbi reality na rasuwar Malam Hashimu. Washegarin sadakar bakwai malam Saleh Baban Hanne ya kirata dakin sa, ya ce ta je ta kwaso kayanta gabadaya, ta kuma yi sallama da Laure ta dawo. Zai cika wasiyyar da marigayi ya bar masa suna hanyar zuwa asibiti. Zai dangana ta da mahaifiyar ta hannu da hannu.... A razane Sa'ade ta dago ta dube shi manyan idanun ta kamar sa fado kasa. Ya gyada mata kai da murmushi a fatar bakin sa ya ce "maza je ki ki dawo, daga yau zuwa gobe, zan sadaki da Innar ki da ta haife ki". **** Tunda suka iso tasha Sa'ade ke rarraba idanu, wannan ne karo na farko da zata fita daga garin Tsanyawa tun tasowar ta. Ita da Hanne rabuwar su mai taba zuciya ce. Tunda suka taso basu taba rabuwa na kwana biyu ba, kullum suna tare dare da rana, yau an ce Jihar Kano zata bari bakidaya ba garin Tsanyawa kadai ba. Zuwa inda bata sani ba, bata taba mafarki ba. Zuwa wajen uwar da bata sani ba, bata taba gani ba. Ko mahaifiyar tata ya zata karbe ta? Ko zata bata matsayin 'ya? Duba da cewa bata taba sanin ta ba? Sai yau a dalilin mutuwa.... mai tonon asiri! Tunaninnikan da Sa'ade ke ta yi kenan a lokacin da suka bar garin Tsanyawa cikin motar Rake Akori-Kura, suka hau titi dodar! Wanda zai sada su da birnin Kano. Hanyar garin ba kwalta a wancan lokacin don haka kura ta turnike idanun su a bayan akori-kurar, sai rufe fuskokin su suka yi da mayafan su. A tashar unguwa uku aka sauke su, inda direbobin suka ce yamma ta yi, zasu yi dare, su nemi waje su kwana in ya so washegari su yi asubanci su samu motar farko. A rumfar wata mai tuwo malam Saleh ya roka mata ta kwana, shi kuma ya kwana a masallacin tashar. Da asubah suna idar da sallah sune pasinjan farko a fasinjojin da zasu tafi garin MAIDUGURI.... ***** "Tafiya yankin azaba". Sa'ade ta fada a zuciyar ta. Sabida yadda ta wahala a motar. Kafin su isa Maiduguri sai yamma lis, duk sun yi wujiga-wujiga daga ita har Baba Saleh. Sau biyu yana saya mata gurasar masu balangu da pure water tana ci a hanya. Shi kam bawan Allah bata tunanin ko loma daya ya saka a bakin sa. Aka sauke su a tashar BAMA, anan ma a tashar suka kwana, da Asuba suka bi mass transiet wadda zata tafi kai tsaye zuwa garin ASKIRA. Sa'ade ba zata manta da garuruwan da suka wuce ba, saboda akwai wani mutum mai yawan surutu a motar tasu, duk garin da aka zo sai ya fadi sunan sa, sun wuce Damboa, sannan suka bulla ta Chibok, sannan Uba, a karshe sai garin da ta ji an kira ASKIRA. (A wancan lokacin ba insurgency, garuruwan Borno lafiya kalau suke). Sa'ade ta daga kai tana kallon garin Askira, garin da aka ce wai anan ne zata ga mahaifiyar ta, wadda ta haife ta, anan take raye. Babban gari ne wanda ya samu cigaban zamani kala-kala a yankin Borno. Koda aka sauke su a tasha tana ji Baba Saleh na tambayar ta ina zai bi ya je gidan Sarki? Sa'ade ta tambayi kanta. Me ya hada mahaifiyar tata da gidan sarki? Bata samu mai bata amsa ba. Da tambaya da kwatance aka kawo su har kofar tankareriyar masarautar Askira. ***** ASKIRA EMIRATE Gidan sarkin Askira koko in ce masarutar Askira babban gini ne a tsakiyar gari, a unguwar da ake kira "unguwar gabas". Tafkeken gida ne mai ginin sama da kasa. Dogarawa ne tun daga zauren farko har zuwa ciki rukuni-rukuni, wasu a zazzaune wasu a tsaitsaye. Daga soron farko za'a cire takalmi duk mai shiga gidan mace ko namiji, ginin farko dake tsakiyar gidan wani irin gidan sama ne wanda ke dauke da kayataccen falo na sarauta wanda anan sarki ke ganawa da bakin sa na nesa. Balcony din dake gefen wajen shine wajen zaman sa tare da mahukunta (king-makers) in ana wani muhimmin sha'ani kamar hawan sallah, nadin sarauta, bikin aure da sauran su. Akwai wata doguwar baranda a kasa wadda anan ya kan zauna a kowanne yammaci ya gana da jama'ar gari yayi musu maganin kukan su, alkalanci da zaman fada. Daga hannun dama na tsakiyar ginin akwai wata babbar kofar katako wadda in ka bi ta zai kai ka barga (ma'ajiyar Dawakai). A kowanne yammaci kyakwawan Dawisu (Peacock) ne a gaban gidan bila-adadin masu ado da ban sha'awa suna baza dogon bindin su cikin nuna baiwar ado da kyau da Allah yayi musu wanda bai yi wa wani tsuntsu ko wata dabba a duniya ba. Akwai fili fetal daga get din farko zuwa ginin farko na shiga ainihin zauren farko na masarautar. Akalla zaka wuce zauruka shida kafin ka tarar da wajen zaman sarki na farko da jama'ar sa na nesa, kafin ka isa wajen zamansa da mahukuntan sa, sannan ka yi tafiya mai tsayi kafin ka shigo ainihin cikin gidan mazaunin iyalin sa. Tsakanin inda sarki ke zama da 'barga' dakunan samarin gidan ne da yara maza da ake riko a gidan, sannan kayi tafiya mai tsayi wadda zata kawo ka get din cikin gida. Bangaren sarki zaka fara taddawa wanda ya hadu da get din cikin gida, kuma akwai kofofi da ke hade da bangaren kowacce matar sa ta aure. Daga gaban ginin akwai baranda mai kama da balcony a gaban kayatacciyar shigifar sarki inda anan ne ya ke ganawa da 'ya'yan sa, matan sa da 'yan uwan sa mata. An fi yin wannan ganawa da yamma ko da daddare. A wannan shiyyar babu mutane da yawa, kowa yana bangaren sa, sai bayi mata wadanda suma suke shige da fice babu yawan surutu, kowacce tana bangaren data ke hidima suna kuma shige da fice daga wannan sassa zuwa wancan na matan Sarki. Sarki kan zauna a kofar shigifar sa da yamma, don gabatar da sallahr la'asar, maza in na jiki ne suna iya shigowa nan, idan 'ya'ya ko jikoki suka shigo a daidai wannan lokacin saidai su rike takalman su a hannu su sunkuyar da kai su wuce in har ba shine ya ce a kira su ba. Amma in a barandar data raba shigifar sa data matan sa yake zaune, da 'ya'yan ko jikokin sun karaso zasu zube gaban shi su kwashi gaisuwa..... "Alanguburo" (Allah ya kara maka yawan rai) shine abinda ake cewa. Ba'a gaida sarkin Askira da "ina wuni? Ko ina kwana?" Shi kuma ya amsa da "Allah Kawun jo" wato kamar ace (Allah yayi albarka). Akasari a wannan shiyyyar babu dogarai babu bayi, in ya ga dama ya kan ja 'ya'yansa da jikokin sa da wasa, yayi musu tambayoyi akan rayuwar su a irin wadannan lokutan. In ka wuce wannan shiyyar ne zaka hadu da bangaren matan gidan. Wato matan Sarki na aure. Kowacce da bangaren ta wadatacce ginin zamani mai manyan shigifu, wanda aka yiwa ado da royal furnishing, babu abinda babu a ciki na jin dadin rayuwa, domin masarautar a zamanance take sannan ilmi ya wadaci al'ummar masarautar, ba abinda zai hada kowacce da 'yar uwar ta in har ba ita ta neme ta ba. Daga bayan nasu bangaren ne na kwarkwarorin sarki ya ke. Ana kiran bangaren kowacce matar sarki da sunanta.....Unguwar Ya Gumsu (Fulani Babba), Unguwar Ya Kirjinoma (Fulani Halima), Unguwar Fulani Hibbani (matar sarki ta uku) sai unguwar Fulani BILKISU (amaryar sarki). 'Ya'yan gidan duk sun girma, mazan na wajen ayyukan su da masu karatu a garuruwa daban daban, matan duk an yi musu aure a masarautu daban daban na jihar Borno, 'ya'yan Hibbani ne kawai 'yan kasa da shekaru sha takwas. 'Yammata ne guda biyu: Naja'atu, da Humaira. Sune kuma kadai ba'a yiwa aure ba a 'ya'ya mata. Kowacce cikin matan sarki tana da manyan 'ya'ya maza da mata, in ka dauke amarya Fulani Bilkisu, wadda har yau take haihuwa suna mutuwa tun suna jarirai wato (wabi). Wannan a takaice shine description na gidan sarkin Askira mai ci a yanzu, da bayanin tsarin masarautar gabadaya. Masarauta ce mai farin jini da tarin arziki wadda aka yiwa shaidar adalci da kyautayi ga talakawanta. Daidai gwargwado 'ya'yan sarki maza da mata sun wadatu da ingantacciyar tarbiyya da ilmin addini da na zamani, duk da ba'a rasa masu fitina ba musamman samarin maza. Kishin da ke tsakanin iyayensu mata bai hana su hadin kai a junan su ba, suna matukar kaunar junan su. Sarki na da 'ya 'ya goma sha biyar, maza da mata da jikoki sama da goma. **** Baba Saleh ya koma gefe ya daga kai yana kallon wannan babbar masarauta da bai taba mafarkin gani a zahiri ba, tun suna yara ya ke jin labarin masarautar Askira, irin tarin arzikin ta da karfin mulkin ta, hannun sa cikin na Sa'ade, sun yi zuru-zuru sabida yunwa da gajiya. Tunanin sa shine wa zai dosa ya ce yana son ganin BILKISU? Wadda marigayi Malam Hashimu ya ce tana daga cikin matan gidan??? Bar ta wadannan dogayen dogaran dake shige da fice suna muzurai kamar sa ci babu, wasu a tsaye kyam kamar an kafe su. Kai sai ka dauka babu bargo a cikin jikin su. Babban abinda ya fi razana shi shine shirgegiyar kofar masarautar, irin kofar nan ce ta jan karfe da ake kira mahdi-ka-ture. Ya ajiye kunshin kayan Sa'ade dake hannun sa a kasa yace da Sa'ade ta hau kai ta zauna, shikuma ya zare sidadden silifan sa ya zauna akai ya kurawa kofar shiga masarautar ido yana tunanin ta inda zai bullo. Kafin ya farga sai ya ga Sa'ade na gyangyadi akan kunshin kayan ta sabida wahala da gajiya. Sai ji yayi wani Dogari ya buga musu gigitacciyar tsawa, "Kai tsoho! Me kuke nema anan?" **** Baba Sale ya mike yana kakkabe kurar jikin sa Sa'ade ma ta yi firgigit ta farka daga gyangyadinta, sai rarraba ido take gabadaya ta firgice. Cikin raunin murya Baba Saleh ya dubi dogarin ya ce. "Mu baki ne tun daga Tsanyawa ta jihar Kano, bawan Allah na zo garin nan ne takanas don in ga Sarkin Askira, don Allah don Annabi ka taimaka mana". Wani wulakantaccen kallo dogarin yayi musu sannan ya ce "ka san wa ka ke nufi kuwa? Tsoho anya lafiya kalau kake?" Baba Sale yayi murmushi mai ciwo irin wanda dan adam ke yi in yana son boye bacin ran sa, ya ce "bani da alaqa da shi, kuma ban zo neman komai wajen sa ba, sakon dana ke dauke da shi na matar sa ne, kaga kuwa bai yi daidai ba in nemi ganin matar sa ba tare da na fara neman alfarmar sa da yardar sa ba. Ka taimaka mana ko don yarinyar nan da ke jin yunwa, marainiya ce". Dai-dai lokacin wani gajeren dogarin ya taso don ganin abinda ya tsayar da dan uwansa wajen wadannan mutanen masu kama da korarrun jeji, "Buba me suke nema ne?" A raine ya dube su sannan ya nuna su da bakin sa "wai maimartaba suke son gani" "amma shine zaka bar su a tsaye ko wurin zama bazaka basu ba?" Ga dukkan alamu shi wannan din mai kirki ne, ya ce da dan uwan sa "maimartaba ya bada damar duk mai son ganin sa ya ganshi cikin kasar sa, cikin aminci da girmamawa, don haka barkan ku da zuwa Masarautar Askira, amma baza ku samu ganin maimartaba ba sai washegarin gobe in Allah ya kaimu idan an fito fada". Baba Saleh yayi godiya sannan ya ce "don Allah ko zan samawa yarinyar nan wajen kwana? Ba mu san kowa a garin nan ba, ni bani da matsala ko a nan wajen zan iya kwana". Wanda aka kira da Adamu wato mai kirkin dogarin, ya ce "ta zo muje in kaita wajen matata ta kwana, kai kuma ka biyo ni". Matar Adamu itama baiwa ce a gidan, bangaren su yana daga can karshen masarautar, unguwa ce guda duk bayi ne da iyalan su, amma yawanci basa wuni anan kowacce tana sassan data ke aiki cikin masarauta, sai dare can suke komawa gidajen su. Ta zubawa Sa'ade tuwo da miyar yauki ta kawo mata ruwa a kofin silba, Sa'ade ta tasar ma tuwon nan kamar Allah ya aiko ta. Sai da ta ci ta koshi matar ta zuba mata ruwa a buta ta nuna mata bayi, taje ta kama ruwa ta fito tayi alwallah ta shimfida mata tabarma anan dan tsakar gidan ta, ta shiga rama sallolin da ke kanta. Ana idar da sallahr isha kuwa barci ya dauke ta akan tabarmar data yi sallar, matar tayi mata shimfida a dakin ta ta tashe ta ta koma daki, ita kuma ta cigaba da ayyukan ta. Washegari ta bata koko da kosai ta karya kumallo, ta sa ta tayi wanka ta canza kaya cikin nata dake kulle, Adamu bai shigo ba sai karfe goma na safe ya ce ta biyo shi. Tayi wa matar da ta ji ya kira Kubra godiya sosai, tabi bayansa, anan waje suka hadu da Baba Saleh ya ji dadin ganin ta cikin kyakkyawar kama, ya karbi kullin kayan ta suka bi bayan Dogari Adamu zuwa fadar sarki. Wuce wannan shigifa, tsallake wannan soro, wuce wannan falo har suka dangana da inda Sarki ke ganawa da jama'ar gari a kowacce rana. Dogarin ya ce su tsaya daga waje, ya shiga ya fadi yayi gaisuwa, sannan ya fadi sakon Baba Saleh, Wazirin sarkin Askira yayi masa tambayoyi a kan su kafin aka amince masa kan ya shigo da su. Baba Sale ya shigo rike da hannun Sa'ade, ya fadi yayi gaisuwa yadda ya ga ana yi, dogarawa suka ce "Sarki ya gaishe ka, ka yi gaggawar fadin abinda ke tafe da kai". Baba Sale ya muskuta sannan ya soma koro bayanin sa cikin nutsuwa, wasiyyar da abokin sa marigayi Malam Hashimu ya bashi a lokacin da yake cikin tsananin ciwo akan gargarar mutuwa, na cewa ya kawo yarinya Sa'ade hannun BILKISU a masarautar Askira idan ta Allah ta kasance da shi. Ya gaya mata cewa diyar ta ce da ta haifa tare da shi a garin Tsanyawa. Sarki Yusufu Bin AbdulHakimu (mai Askira), ya dan zamo daga cikin kujerar mulkin sa ya tsurawa yarinyar ido, wadda ke sanye cikin ragga, 'yar kauye futuk, ya shiga tunanin ta inda ta fito daga jikin matar sa mafi soyuwa a gare shi, ya san ta taba aure kafin ya aureta, amma bai taba sanin tana da 'ya ba, bata taba gaya masa ba.... Sai dai ido, hanci da baki kadai sun nuna zahirin kamannin Fulani Bilkisu a tare da yarinyar. Jini baya taba buya. Har lange-langen jikin. Musamman data dago manyan idanunta tana kallon sarkin, sai ya ga kamar Bilkisun ce ke duban sa da manyan fararen idanun ta. Magana yayi kadan da Wazirinsa, shi kuma ya yiwa bafaden dake gefensa magana, sai bafaden yace da Baba Saleh su biyo shi. Wani hamshakin falo ya kai su can hanyar shiga cikin gidan, falon bai cika girma ba, amma ya sha adon kayan fata na sarauta dasu tum-tum, dogarin ya ce su zauna anan, su jira rabin awa. Daga Sa'ade har Baba Sale ba mai magana, sai kalle - kalle suke mai nuna kauyancin su tifikal, zuwa can Baba Sale ya nisa ya ce. "Sa'ade! Ko me kika ga ya faru da bawa haka Allah ya ga damar ya kasance a gare shi, idan mahaifiyar ki ta karbe ki shikenan, idan bata karbe ki ba, ni zan rike ki tare da Hanne a cikin iyali na har iyakar nawa numfashin". Daga yadda yake magana zaka gane ya karaya, bai san girman masarautar da kasaitar ta ya kai haka ba! Bai san sarautar babba ce irin wannan ba! Ya dauka normal sarkin kauye ne irin wanda ya sani. Masarautar Askira kuwa tana cikin manyan masarutun jihar Borno masu tsohon tarihi da yalwar arziki wadanda ke sahu na biyu a jihar ta Borno bakidaya. Sa'ade cikin rawar murya ta ce "Baba Sale ni dai mu koma Tsanyawa.... ko ta karbe ni bazan iya zama a gidan nan ba tsoro nake ji....wallahi bazan zauna ba". Baba Sale cikin lallashi ya ce "ki kwantar da hankalin ki Sa'ade, idan ta karbe kin shine babban gatan ki, kin ga ni na tsufa, ko zan rike ki na dan lokaci ne nima wa'adina zai cika, baki da kowa a Tsanyawa bayan ni da Innar Hanne, aure zai yi miki wuya don kuwa babu wanda ya san asalin iyayen ki". Yana rufe baki suka ji ana "gyara kimtsi mai Askira......taka lafiya Giwan Askira.....". Sarki ya shigo falon shi kadai, dogarawan suka tsaya daga waje. Kujerar sa wadda ita kadai ce kujera a falon ya je ya zauna. Baba Sale ya fadi kamar zai yi sujjadah yadda ya ga ana yi ya kara gaida sarki, sarki yai masa murmushi ya amsa da wata irin hamshakiyar kamilalliyar murya. Ya mika hannu ya yafito Sa'ade, "zo nan kusa gare ni diya ta". Sa'ade ta rarrafa ta isa gaban shi, ya dora hannu a kanta ya ce "yaya sunanki?" Murya na rawa ta ce "Sa'ade!" Yayi murmushi ya ce "Sa'adatu dai ko? Sannu da zuwa Askira kin ji Sa'adatu?". Sannan ya maida hankalin sa ga Baba Saleh yace ya bashi labarin rayuwar Sa'ade a hannun mahaifin ta tun daga sanda mahaifiyarta ta bar ta. Baba Sale ya gaya masa duk irin abinda ya sani cikin nutsuwa akan Sa'ade da Baban ta, da irin yadda yadda ya raine ta cikin tsananin kulawa, ya gaya masa malam Hashimu ya gaya masa ba don rayuwa da yake zaton ta kare masa ba bazai taba baiwa Bilkisu 'yar sa ba, sabida bai taba jin dadin zama da ita ba har auren shekara biyu ya shiga tsakanin su ya kare a shekaru biyu kacal. Ya gaya masa wahalar da yarinyar ta sha a hannun matar uban ta, da yadda ta kare rayuwar ta a talle. Sarki Yusufu ya kara jan Sa'ade jikin sa yana tunani cikin ransa "anya Bilkisu ce da ya sani? Zata haifi Da ta tafi ba waiwaye shekaru goma sha biyu? Kuma bata taba gaya masa ba daidai da kuskure, ya san dai a bazawara ya aureta amma bai san komai ba bayan wannan akan auren nata na baya. Bata son zancen ko kadan. Shi kuma nan duniya sai ya samu zuciyar sa da matsananciyar kaunar Sa'ade, wadda tausayi da soyayyar uwar ta shine sila. Ya tambayi Baba Sale asalin malam Hashimu, Baba Sale yace "kowa ya san Malam Hashimu bakon haure ne a Tsanyawa babu wanda ya san asalin sa, amma a sanda yake bashi wasiyyar kawo Sa'ade wajen Innar ta ya gaya masa shi dan asalin garin Damaturu ne. Daidai lokacin da aka daga labulen falon, ta shigo cikin taku na kasaita, sanye cikin farar alkyabba da hular alkyabbar a kan ta. A kasan alkyabbar wani kasurgumin bakin leshi ne mai matukar nauyi. Doguwa sambaleliya, fara sol, kamar da ka taba ta jini zai yi tsartuwa. Fatar jikin ta a murje, ga tsayi ga zati, sannan ga kira ta matan Shuwa-Arab tattare da ita. Akwai barima ta danyen gold makale a gefen hancin ta. Manyan fararen idanun ta sun sha 'kohl' sai walainiya suke suna fidda wani sheki na musamman. A hankali take taku har ta isa gefen mijin ta ta zauna. Kuyangin ta suka tsaya daga waje. Ta bi mutanen dake sunkuye a gabansa da kallon mamaki, don sun fi kama da normal talakawan gari, amma a falon ganawar sarki da iyalin sa? Kuma saboda su ne aka kirawo ta? Idanunta suka kai ga birkitacciyar bakauyiyar yarinyar dake zaune gefen sarki, ya rike ta cikin jikin sa. Ta tsurawa yarinyar manyan idanun ta tana kallon ta, idanunta a hankali suke kara girma suna fidda mamaki da al'ajabi. Da gaske ne da aka ce duk inda uwa ta ga dan da ta haifa cikin kowanne hali sai jikin ta ya bata. Babu wanda ya ce mata uffan tsakanin sarki da Baba Saleh, har saida ta dauke idon ta daga kan yarinyar ta sunkuyar. Wani abu yammmm! Na bin jikin ta. Tsigar jikin ta na tashi. Ta kifa fuskar ta cikin tafukanta, cikin zuciyar ta take fadin...... "dama na san ko bajima ko ba dade zata zo ne da kafafun ta, muddin ni na haife ta. Amma ban zaci a wadannan kananan shekarun ba, na dauka dai sai ta mallaki hankalin kanta zata kawo kanta". Sarki Yusufu ya kama hannun Sa'ade ya sanya cikin nata. Expression na fuskarta kadai ya gaya masa duk abinda Baba Saleh ya fada gaskiya ne. "Jeki ga mahaifiyar ki Sa'adatu, ki ji dumin jikin ta, kamar yadda kowanne da yake jin dumin jikin uwar sa". Sa'ade ta kasa yin hakan, ganin yadda matar ta cire hannu daga fuskar ta ta bubbude mata ido, kamr tana gargadin ta da yin hakan. Ta dubi Baba Saleh da kakkausar murya tace. "Kai dan aiken Hashimu! Ka koma ka gaya masa yadda Bilkisu bata taba son sa ba, haka bata son abinda ya fito daga jikin sa, bana bukatar 'yar sa ya cigaba da rikon abar sa shi kadai". Sa'ade ta fashe da kuka, Baba Saleh kuma ya sunkuyar da kai. Sarki Yusufu ya daga ido cikin firgici ya dube ta, anya Bilkisun sa ce wannan? Wadda ko barorin ta bata dagawa murya tsakanin ta da kowa kyautayi ne da mutuntawa? Balle dan da ta haifa? Dan da kullum take adduar Allah ya bar mata ko guda daya? "Ko da Hashimun ya mutu bazaki rike 'yar da kika haifa ba?" Muryar sarki akwai fushi da fusata mai tsanani a cikin ta a lokacin da ya jefe ta da wannan kalami, mikewa tayi tana shirin barin falon ko kadan zuciyar ta bata russuna ba, "idan ya mutu yana da dan uwa a garin Damaturu, a kai ta can ya rike masa". Har ta kai bakin kofa sarki ya kira ta da kakkausar murya... "FULANI BILKISU!" Ta dakata, amma ba tare da ta juyo ba. "Zo ki kama hannun 'yar ki ki tafi da ita sassan ki, ki bata duk kulawar da uwa zata baiwa danta, tana karkashin amana ta, zamana zata yi a gidannan daga nan har karshen rayuwar ta, a bisa kulawa da kiyayewa ta". Yana fadin hakan ya mike tsaye, ya dubi Sa'ade da ke kuka wurjanjan, "daina kuka Sa'adatu, mahaifiyar ki ce bazata cutar da ke ba, dauki kayan ki ki bi bayan ta". Sa'ade ta share hawayen ta da bayan hannun ta, ita in aka ce wannan galleliyar matar mahaifiyar ta ce ma wani iri take ji, tsigar jikin ta har tashi take, tsoron ta take ji sosai, gata da manyan ido da wani irin kwarjini, ita gara ta bi Baba Sale su koma Tsanyawa, abinda ta fada cikin kuka kenan, amma Baba Saleh ya girgiza mata kai ya ce. "Bi ta Sa'ade, kiyi mata biyayya a bisa dukkan umarnin ta, aljannar ki na tare da ita". Ta dauki tsummokaranta tana waiwayen Baba Saleh, shikuma yana yi mata murmushi, tuni Fulani Bilkisu ta fice, kuyangin ta sun mara mata baya, sai da ta hada da gudu-gudu ta cimmasu, Sarki Yusufu yace da Baba Saleh za'azo a kai shi masauki ya huta har zuwa iya kwanakin da ya ke so, sannan zai sa a maida shi har Tsanyawa a motar gida, zai bada sallama a bashi, Allah ya kai shi gida lafiya, yana yi masa fatan hutu mai dadi cikin masarautar sa. Baba Saleh ya zube yayi ta godiya, a take dogarawa suka kai shi masaukin bakin sarki, aka wadata shi da abinciccika da ababen sha na alfarma, sittiru da duk abinda zai bukata. Amma duk wannan bai dame shi ba, tunanin sa na ga halin da Sa'ade zata kasance a hannun mahaifiyar ta. Wadda ta nuna a fili bata bukatar ta cikin rayuwar ta. Bai san laifin da Malam Hashimu yayi mata ba, amma ya lura kiyayyarsa ce ta shafi 'yar sa. Abu daya yake da yakini yake kuma dan kwantar masa da hankali idan ya tuna ita ta haifeta da gaske, duk kin ta da ita bazata cutar da ita ba, sai dai ta kasa nuna mata soyayya. Yana tausayin Sa'ade sabida bata taba dandana kaunar UWA ba, bata taba jin dumin uwa ba, ga wahalar data sha hannun Laure, sannan yanzu ga ta ga uwar amma bata kaunar ta. Zuciyar sa tayi maza ta ce masa "ba ita ce bata so ba uban ta ne bata so, da sannu in sun zauna tare Allah zai musanya zuciyar ta zuwa alkhairi akan 'yar ta".. Da kyar ya samu ya runtsa a wannan dare sabida tunanin Sa'ade, hutun da aka ce ya zauna yayi ya ga bazai iya ba, washegari ya gayawa mai kula da shi ya gayawa maimartaba yau zai koma garin su. Sarki yasa aka yi masa goma ta arziki, aka cika masa bayan mota hilux, sannan ya damka mishi kyautar kudi da sittiru masu yawa. Suka kama hanyar zuwa Tsanyawa a mota hilux zuciyar Baba Saleh cike da alhini na tausayin Sa'ade. **** Sa'ade na bin kuyangin Fulani a baya, fada nan fada can har suka dangana da wani babban gini, kamar gida guda bangare guda haka, aka bude kofar Fulani ta sanya kafar ta kamar wata Dawisu sabida yadda take taku su kuma suna biye da ita, kyawu da kayatuwar ginin yasa Sa'ade sakin baki da hanci tana kallo, har tana tuntube saura kadan ta fadi. Manyan faluka suka rika wucewa har suka tadda wanda daga shi kuyangin suke da shamaki, sai guda daya daga cikin su ce ta bi bayan Fulani, bata jima ba ta fito tace da Sa'ade wadda ta tsaya a inda ta ga kowa ya tsaya itama, ta biyo ta ta kai ta dakin da zata zauna. Inda Fulanin ta shiga nan ta ga sun shiga, wani (english parlour) ne komai fari sol har labulaye da kujeru, kilishin falon ne kawai launin makuba shima da adon fari da baki a jiki, kofofi ne wajen guda hudu a falon bata san a wanne Fulani ke ciki ba, kuyangar ta bude daki daya suka shiga. Sa'ade ji tayi numfashin ta ya tsaya a wuyanta sabida kyawun dakin da tsaruwar sa, komai dake cikin dakin kalar blue and light pink ne, ga wani shimfidadden gado na sarauta (royal bed) da ya ji shimfidu na alfarma. Kuyangar ta shiga bandaki ta hada mata ruwan wanka, tazo ta kama hannnun ta ta kaita har gaban kwamin wankan, ta nuna mata yadda ake amfani da komai don ba sai da bayani ba kallo daya za'ayi wa Sa'ade a fahimci bata taba alaqa da irin wannan muhallin ba a rayuwar ta. Ta kasa boye firgici da razanar data ke ciki. Kuyangar tace zata cuda mata baya. Sa'ade ta zaro ido tace "bana so". Ta fita ta barta bayan ta tattare tsummokaran data tube ta hada da kullin kayan ta ta fita dasu ta zubar kamar yadda Fulani ta bata umarni. Kafin Sa'ade ta fito ta ajiye mata dogayen riguna daidai tsayin ta guda biyu a gefen gado, sannan ta shigo mata da abinci lafiyayye kala kala akan tray. Ta zauna har ta fito daga wankan daure da tawul din data nuna mata sannan ta gaya mata nan ne dakin ta, ba koyaushe zata ga Fulani ba, in tana son ganin ta zata nemeta da kanta, ba'a yarda taje ko'ina bayan dakin nan ba, duk abinda take so ita kuyangar zata dinga shigowa tana yi mata, ta gaya mata cewa itace amintacciyar Fulani, kuma ita kadai ke shigowa wannan sashen, sunan ta "Fanna". Sa'ade ta gyada mata kai alamar ta gane, sannan ta ce da ita "ga hijab nan da darduma kiyi sallah". Bayan fitar Fanna Sa'ade zama tayi a bakin gadon a dofane tana ta kallon dakin, sai ta ji duk alatun dake cikin sa bai burgeta ba, ta ji duniya tayi mata kunci, kewar Baban ta mai son ta, ta zo ta lullube ta. Soyayyarsa ta fi mata duka wannan alatun da babu soyayya a cikin sa sai kiyayya zallah. Amma duk da wannan damuwar dake cin ranta, ba abinda zuciyar ta ke hango mata sai fuskar Fulani Bilkisu ma'abociyar zati da kamala, da wani irin feelings mai fizgar zuciya tamkar maganadisu (maternal love). Wata irin soyayya da bata taba ji akan kowa a duniya ba bayan Babanta, wannan soyayyar har ta zarta wadda take ji akan Baban ta. Shine abinda ta ke ji akan Fulani Bilkisu! Ta lumshe ido tana hasaso yadda ta zazzaro mata ido kada ta zo kusa da ita, a kuruciyar Sa'ade ba don komai bane sai don ita 'yar kauye ce. Tana kyankyamin ta ne kawai. Tasa a ranta daga yau kullum zata dinga wanka, don Fulani ta daina tsantsamin ta. Ta mike ta sanya hijab ta tada birkitacciyar sallarta, wadda ko kadan ba daidai take yin ta ba, sannan babu wani karatun sallah na azo a gani, karewa ma "BA-SIM-MI'ARA" take karantawa a cikin sallahr. Data idar da azahar da la'asar sai ta ja farantin abincin da Fanna ta ajiye mata, ta ci iya cinta kunnenta kamar ya gutsure don dadin naman tolo-tolo, data gama ta je ta wanke hannu ta dawo ta kwanta a gadon da tun dazu take son ta ji yaya yake? Wane irin laushi gareshi haka da tun dazu ya ke fizgar idanun ta? Wani barawon barci yazo yayi awon gaba da ita, sau biyu Fanna tana shigowa, ta fidda farantin ta kunna mata iyakwandishan wanda ni'imar ta ya kara armasa mata barcin. **** Sai safah da marwa take a dakin barcinta, ta kasa barci, ta rasa abinda ke mata dadi. It's very unusual maimartaba ya shigo sassan matan sa. Amma yau sai kawai ta ganshi ya shigo har dakin barcin nata, ba zaton ta ba tsammani. "Zuwa nayi ki gaya min abinda matsayi na bai kai na sani ba, wanda ya faru cikin rayuwar ki ta baya". Ya fada yana mai zama a gefen hamshakin gadon ta. Gabadaya ta zama upset, daga rana zuwa dare, fuskarta kamar jikakkiyar takarda, ta zama yellow, kasancewar ta jazur, damuwa kwance baro-baro, ga wani tsohon kwantaccen bacin rai da ya dawo mata sabo. "Allah ya huci zuciyar ku, Allah ya huci zuciyar Askirama!". (Askirama na nufin 'mai Askira' da harshen Kanuri). Ta cigaba da fadin "Al'amarin bashi da muhimmancin da zaku san shi, shi yasa baku san shin ba. Sabida ban taba daukar sa da muhimmanci ba, ban kuma taba zaton wannan 'yar zata biyo ni ba, don nasan uban ta ko za'a dora masa wuka a makoshi, akan ya bani ita, ba zai taba bayarwa ba". "Sai kuma mutuwa ta yanke muku dukkan kudirin ku ke da shi, akan baiwar Allah, wannan ya isa ya nuna muku cewa karfin kudura da irada naShi ne, bawa bai isa ya tsarawa kansa rayuwa ba, face abinda Ubangiji ya tsara masa". Mai martaba ya fada mata a tsanake. Ta sunkuyar da kanta, tana wasa da yatsun hannun ta, bata ce komai ba. "Ki gaya mini duk abinda yakamata na sani akan yarinyar nan, tunda dai kin yarda sunnah ki kai kika haifeta, kada ki zama azzalumar Uwa, wallahi Allah bazai bar ki ba". Fuskarta tayi jajawur kafin hawaye su cicciko idon ta. "Ran ka ya dade bana son tuna labarin nan, bana so. Ba abun fade a cikin sa, me kake so ka ji? Yes, aure na yi na haife ta, amma ban taba son uban ta ba! Sau daya ya taba kwanciya da ni bisa fin karfi har na samu cikin ta. Kana so ka ji cewa Babana biyan bashi yayi wa ubanta da ni? Ya aura masa ni a matsayin filin sa da yake bin sa bashi?" Maimartaba ya nuna abin bai bashi mamaki ba, a fuska da muryar sa babu komai, yace "to ita yarinya meye laifin ta? Bata zo duniyar ba lokacin, balle ta san laifin da babanta ko baban ki yayi miki da zaki rama a kanta. Ki yi a hankali, 'ya'ya amanar Allah ne a hannun mu, bar ganin ke kika haifeta, wallahi hakkin ta zai iya kai ki wuta. Ba kya tunanin hakkin ta ne yake hana wadanda kike ta haifa rayuwa? Tunda itama baki ji kanta ba a lokacin da Allah ya baki ita?" Bata ce komai ba amma tabbas kalaman sa sun shige ta, daga zaunen da yake ya kamo hannun ta. "Bilkisu ki karbi amanar da Allah ya baki da hannu bibbiyu, na yafe jin labarin auren ki da mahaifin ta tunda na lura yana tono miki bacin rai ne, wanda kika riga kika manta. Abu daya nake so ki rike a ranki shine wannan yarinya dolen ki ce, bata da sauran gata sai ke, wani dan uwan baban ta da kika ce akwai a Damaturu ba shi shari'ah ta bawa rikon ta ba kasacewar ta mace, kuma kina raye, sannan kina da halin rike ta. Ni na karbi yarinyar nan kamar sauran 'ya'ya na..... idan ni da nake kishin Baban ta ya riga ni samun ki, na karbi 'yar sa zan rike da amana, ke mai zai hana ki kwatanta tausayi da adalci irin na UWA ki karbi marainiyar Allah???" Sai ta fada jikin sa tana kuka sosai, jikin ta yana tsuma, ya rike ta sosai a jikin sa yana cigaba da lallashin ta, Fulani Bilkisu ta san maimartaba yana son ta, amma bata zaci son ya kai har haka ba, duk da bata taba haife masa rayayyen Da ba. Shi gashi yau ya karbi nata da hannu bibbiyu, wanda bai taba sanin da wanzuwar sa ba. Idan bata yi masa biyayya ba kuwa, hakika ta cika butulu, wadda bata godewa ni'imomin Ubangiji gareta ba. "Zaki kula da ita ko Bilkisu? Zaki bata kaunar duk da ya kamata ki bata?" Ta gyada masa kai, ba tare da ta ce komai ba. Sai rungume shi data yi sosai a jikin ta. "Ka yi min alfarma Askirama kar ka gayawa kowa cewa 'ya ta ce, don Allah, kace 'yar kanwata ce na karbo, ina gudun gorin kishiyoyi, tunda cikin su babu wadda ta san na taba aure kafin na zo gidannan". "In don wannan ne kada ki damu, amma akwai wadanda sun riga sun ji a fada, zan gargadesu don duk na san su". "Nagode.... Nagode Askirama. Alanguburo (Allah ya kara maka yawan rai)". **** Duk da haka sai da ta kwashe kwanaki uku bata nemi Sa'ade ba, bata shiga dakin ta ba, bata nemi sanin halin data ke ciki ba. Fanna dai ta gaya mata tana nan lafiya kuma tana kokarin koyar da ita tsafta da sauran abubuwa. Sarki Yusufu ya san halin kafiya irin na Bilkisu, don haka bai gushe ba yana cigaba da lallashin ta akan Sa'ade. Tana nuna masa komai lafiya, alhalin bata kara sanya yarinyar ma a idon ta ba. A rana ta hudu sai gashi ya kara dawowa da kansa da safe kafin ya fita zuwa zaman fada. Tana karya kumallo ita kadai a 'dining table' din falon cin abincin ta. Ta mike cikin girmamawa ta same shi a kujerun da suka kawata falon, suka gaisa kamar yadda suka saba cike da kewar juna kasancewar ba ita tayi girki ba, kwana biyu kenan basu hadu ba, cikin hikima irin ta manya ya ce, "Yaya kike cin abincin ke kadai babu 'yar tayin hira? Maza kirawo min ita mu gaisa, sabida ita na shigo". Fuska a turbune tace "bata tashi daga barci ba" "A taso ta" Ba yadda ta iya dole ta juya cikin kasaitaccen takunta ta nufi dakin da ta san ta ce a ajiye mata Sa'aden kamar wani kayan wanki. Ta murda kofar ta shiga a hankali ba tare da ta bari sauti ya fita ba, akan darduma ta same ta tana sallah, tana wani karatu a fili "basim-mi'ara, alu ambaki wau-zal, wa'aluba ilallan haakuri"..... sannan ta tafi sujjadah ba tare da ta yi ruku'u ba. Fulani ta mutu a tsaye, sujjadar ma guda daya tayi ta sallame sallahr. Kamar jikin ta ya bata da mutum a dakin, da sauri ta juyo, suka hada ido da matar data ke kwana tana wuni da ita a ran ta. Da kyar Fulani ta hada sautin muryar ta waje daya, ta ce "sallahr me kike yi?" "Asubah ce Inna" "Asubah? Wa ya ce miki yanzu ne lokacin sallar asubah karfe goma na safe har ta wuce?" "Ai i yanzu nake yin ta kullum, wataran ma sai na dawo daga talla ma nake hadawa da azahar inyi kafin Baba ya barni na fara zuwa makarantar A-BA-CA-DA". Takaici ya hanata magana kawai ta juya a fusace tare da cewa "biyo ni". Suna shigowa falon taga maimartaba a zaune cikin rawanin sa da jabba, da sauri ta tafi gareshi ta zube a gaban sa, ta lura shi mai kirki ne ba irin matar sa ba mai kama da mala'ikun daukar rai. "Baba ina kwana" yayi murmushi yana kallon ta da tausayi "Anan ba'a cewa Baba diyata. "Alanguburo" ake cewa. Tayi kokarin maimaita kalmar amma ta kasa. Yayi dariya kadan cikin tausayi yace "kina son makaranta?" "Sosai Alan...." sai ta yi shiru. Ya karasa mata "......guburo" ta maimaita a hankali "Alanguburo" "masha Allah! Makaranta wacce kike so? Ta kwana ko ta jeka ka dawo?" Ta saci kallon Fulani Bilkisu ta ga yadda take hararar ta, sai ta ga ai gara mata ta zabi makarantar kwana akan zama ita kadai cikin daki da idanun Innarta masu razanata. A hankali ta ce. "Na fi son makarantar kwana Alanguburo" "To shikenan tashi jeki abun ki, nan da sati biyu za'a kai ki, amma bazakiyi nisa da gari ba, nan cikin garin Maiduguri zan sa a nema miki mai kyau, ince ko kina kunna talbijin kina kallo?" "Menene talbijin Alanguburo?" Ya nuna mata ita da hannu, ta ce "ai babu a dakin dana ke" ya ce "Innar ki bata kyauta ba, yau zan sa a kawo miki taki a jona miki a dakin ki". Ta hau murna sosai ta ce "Nagode Alanguburo" Yace "Allah Kawun jo". **** Duk yadda ta so ta wuni cikin sukuni a ranar ta kasa, sallahr Sa'ade da karatun sallahrta kawai take tunowa. Hankalin ta ba karamin tashi yayi ba, wai dan musulmi ne yake irin wannan ibadar, me ake da rayuwar jahilci. Ta so ta share, don a ganinta tunda Askirama ya ce zai kaita makaranta ta san zata koya a can, amma sati biyun da zata cigaba tana irin wannnan sallahr zuwa lokacin da zata koya din shin idan ta bari Allah ba zai tambaye ta ba? Tunda har ya nufe ta da gani, tamkar umarni ne ya bata kan ta yi mata gyara tana so ko bata so, ita ba jahila bace ta san muhimmancin sallah ga dan musulmi, balle wanda ka haifa a cikin ka. Ta kira Fanna da zata wuce kai mata abincin dare, tace "kira min yarinyar can ta same ni a dakina yanzun nan". Fanna ta yi matukar mamaki don banda ita Fannan ba mai shiga dakin Fulani Bilkisu, itama gyara ne kawai yake kai ta shima ba kullum ba, sai lokacin da Fulanin ta bukata. Har dakin ta kawo Sa'ade, sannan tayi bankwana ta juya, don ta gama aikin ta na daren sai kuma gobe. A wannan lokacin ne Fulani ta yi mata kallo na sosai, tana durkushe gabanta kamar yadda ta ga Fanna na yi, da can a fizge take kallon ta, a 'yan kwanaki hudun kacal data yi cikin gidan har ta fara washewa, kamannin ta da ita sun gigitata, kallo daya zaka yiwa yarinyar ka san ita ta haifi abar ta, kamar ta yi kaki ta tofar. Anya akwai wanda zai yarda in aka ce ba 'yar ta bace? Ko dai ta bari Askirama ya fadi gaskiya ne? Amma in ta tuna gorin da zata sha wajen Ya Gumsu (most senior wife ta sarki) kuma wadda suke buga mugun kishi da ita fiye da sauran matan sarki sabida yadda take jin kanta matsayin uwar manyan 'ya'yan sa, amma ya zo yana fifita Bilkisu akan ta, wanda hakan ya haifar da zazzafan kishi a tsakanin su, sai ta ga gara ta bar ta a 'yar kanwar ta ce, ai is normal dan dan uwanka yayi kama da kai. Ta yi ajiyar zuciya tareda dauke kanta daga kallon yarinyar tana jin kirjin ta na wani irin bugawa, inta kalli yarinyar sai ta tuno sanda Hashimu ya daure ta a jikin karfen gado ya haike mata, ko ta so ta ji tauayin ta abinda take tunawa kenan ta ganta bakikkirin a idanun ta, duk da an ce ya mutu, bata jin nan kusa zata yafe masa, ta hadiye wani kullutu daya tokare ta a kahon zucci, tana mai kautar da kanta ta ce mata. "Kin yi sallahr Isha?" "A'ah Inna, bari nayi sai can dare, an ce sallah cikin dare tafi lada" Ta galla mata harara tace "inji uban wa? Ni kar ki sake ce min Inna". Sa'ade ta yi shiru tana kikkifta ido. Ta nuna mata hanyar toilet da hannun ta "muje ki yi wankan sallah da alwalah akan idona na gani" Sa'ade ta zaro ido. "Kina nufin a gaban ki zan yi timbir?" Ta sake galla mata harara cikin tsawa tace, "Rufe min baki! Ko kin ga ana yi min musu a gidannan? Zaki wuce ko sai na hankada ki?" Sum-sum-sum Sa'ade ta wuce ita kuma ta bi bayanta. Da kyar Sa'ade ta iya cire riga a gaban Fulani, tana yi tana kare kirjin ta, tace tayi wankan tsarki tana gani. Ai yadda ake normal wanka da soso da sabulu haka Sa'ade ta yi, alwala kuwa ba'a zancen ta. Fulani Bilkisu ta ji kwalla ta tarammata, ba na tausayin yarinyar bane na tunanin wai gudan jinin ta a duniya ne wannan ba arabi ba boko. Zama tayi akan masai ta dinga gaya mata yadda zatayi wankan tsarki don ta tambayeta cewa ko ta fara ganin jinin al'ada ta tabbatar mata ta fara, sannan ta koya mata alwala, suka fito ta bata mayafi tace ta tsaya ta lura sosai da yadda take sallah. Sannan tasa ta tayi tana kallo. Akwai improvement sosai duk da haka wani abun sai kyalewa ta yi, ta san a hankali zata kara gyarawa. Sannan ta zaunar da ita a gaban ta ta koyar da ita fatiha, falaki da nasi da ikhlas, cikin 'yan mintuna Sa'ade ta karanta mata su tiryan-tiryan, daga nan ta gane tana da saurin daukar abu muddin zata samu kulawa. Sai karfe goma na dare ta sallameta. Bayan ta gaya mata wannan karatun data koya mata yanzu ta karanta ta tofa a hannayen ta ta shafe jikin ta da shi. Daga ranar kuma bata kara nemanta ba, sai bayan sati guda, shi din ma kayane akwati uku maimartaba ya aiko mata dasu, atamfofi, lesuka da shaddoji na alfarma, ta sa telar ta tazo har sassan ta ta gwada yarinyar a gabanta, don har zuwa ranar ko kofar falo na biyu bata bari ta fita ba, Allah Allah take ma satin ya zagayo a kaita makarantar kwanan ta huta. Ta manta cewa magana bata buya a gidan sarauta, abinda bata sani ba kuyangi suna magana a junan su cewa yarinyar nan da aka kawo daga kauye tun ranar da ta zo basu kara ganin ko inuwarta ba kuma basu san daga ina aka kawo ta ba ko aikin me ta zo yi. Har tsakanin kuyangin sauran matan sarki suna zancen har zance ya kai kunnen su Ya Gumsu, Ya Kirjinoma da Fulani Hibbani cewa Fulani Bilkisu ta dauko rikon 'ya daga kauye. Ya Gumsu tace "matar so an gaji da zaman kadaici an buge da tsinto 'ya'ya". Ita kuwa Hibbani cikin hila ta tambayi Askirama ko ya san da batun 'yar da Bilkisu ta dauko riko? Ba tareda ya bata hankalin sa ba ya ce 'yar kanwarta ce, kanwar tata ta mutu". Haka ta je ta fesawa Ya Gumsu, ita Ya Kirjinoma dama bata shiga sha'anin su, daga ita sai 'ya'yan ta take harkokin ta, tana da kamun girma sosai. A cikin sati biyun kafin tafiyar Sa'ade makaranta akwai cigaba sosai a tare da ita, sallahrta ta gyaru, ga wanka ya kama jikin ta, Fanna ta koya mata yin Brush sau biyu a rana, safe da dare, ta zama kamar Yayarta. Har hira suke yi sosai in Fulani ta tafi girki Turakar Sarki. Tana kara gyara mata kome ta ga ta yi ba daidai ba, har dige-digen data ke yi a fuskarta da kwalli Fanna ta hana ta. Sannan ta kiyaye umarnin uwargijiyarta da gaskiya na cewa kada ta bari kowacce kuyanga ta zo inda Sa'ade ta ke, bata yarda tayi alaqa da kowa cikin sassan ba bayan ita Fannar. Ana i gobe sati biyun da Sarki yayi alkawari ya sake shigowa sassan nasu, wannan karon da daddare. Ya samu Fulani da kuyanginta kusan su duka goman ana bata labarai tana murmusawa. Yana shigowa duk suka mike, fadi suke in chorused "...zauna daidai mai Askira... takawar ka lafiya Askirama!" Suka fice akan layi, shikuma ya zauna sannan ya soma yiwa Fulani fada. "Haka kawai kin kama yarinya kin kulle a daki don mugunta, kin hanata ko zama cikin kuyangin ki, to wadanda kike gudun su san da zamanta sun riga sun sani, gara ma ki sakarwa yarinya mara ta yi fitsari". Ita dai bata ce komai ba sai "Allah ya huci zuciyar Askirama (mai Askira). Bai amsa ta ba ya ce "kira wo min Sa'adatu". Ta tashi tana tafiyarta cikin yauki na halitta ta nufi dakin Sa'ade. "Ke ki zo ana kiran ki". Ta ce da Sa'ade wadda ke luntsume tsakiyar gado ta kafawa talabijin ido tana kallon diramar larabawa. Irin yadda ta saki baki da hanci tana kallon ba karamin haushi ya baiwa Fulani ba. Kamar tayi fiffike ta shige cikin akwatun talbijin din a yi da ita. Ko maganar Fulani bata ji ba, sai da ta taka ta kashe soket din talbijin din, tayi firgigit tace "haba don Allah Inna ya zaki kashe mini.....?" Sauran maganar ta makale mata a makoshi sabida mugun kallon da Fulani ta jefe ta da shi. "Na ce ki zo, ko ke kurma ce ne?" Sa'ade ta sauko daga gadon ta bi bayan ta don tuni har ta fice, tana shigowa falon ta yi arba da Sarki, ai tuni ta washe ta daina fushin kashe mata talbijin da Fulani ta yi ta nufi wajen sa cikin tsananin murna. "Alan....ina wuni?" Yayi murmushi ya yafito ta da hannun sa. "Zo nan kusa gare ni Sa'adatu" ta rarrafa gabansa ta zauna ya ce "Ah! Masha Allah, da alama Fulani tana kula da ke, gashinan kin yi haske kin yi kumatu" ta saci kallon Fulanin, hararar data ke mata yasa ta kasa fada masa abinda ta yi niyya, cewa ita bata wani kula da ita, Fanna ce take kula da ita, ita sai tayi kwanaki bata ko ga inuwar ta ba. Aka soma shigo da kwalaye da katon katon na kayan masarufi ana jibgewa a gefe. Daga ita har Fulani Bilkisu bin kayan suka yi da kallo don basu san ko na menene ba. "An samo makarantar Sa'adatu, an gama komai, gobe za'a kaita, ita da zuwa gida sai karshen kowanne zangon karatu, sai kuyi sallama yau, don gobe da sassafe za'a kai su ita da Humaira". Fuskar Fulani ta tattare cikin rashin jin dadi, bata son a alaqanta komai na Sa'ade da 'ya'yan gidannan, ba don komai ba sai don gudarwa kanta gori. Balle 'ya'yan Hibbani sarakan surutu, ita kuma Hibbanin uwar tsugudidi, in taji abu to tabbata Ya Gumsu ta ji ta gama. Amma ai da kunya tace masa bata so ya hada 'yar ta da 'yar sa, shi da yayi wannan kara ta mutuntawa in ba'a gode masa ba akalla baza'a kalubalance shi ba. "Allah ya kaimu" Kawai ta ce. Sa'ade ta dago cikin farin ciki ta ce "Alan....amma inna tafi sai bayan shekara zan dawo ko?" Cikin mamaki yace "ba kya marmarin ganin Innar ki zaki yiwa kanki fatan yin shekara a makaranta?" Ta sunkuyar da kai a ranta tana so ta gaya masa ita Innar ce bata son gani kusa da ita da wadannan muzuran idanun nata masu karkada mata 'ya'yan hanji, sannan kadaici yana damun ta, banda yanzu da aka jona mata talbiin take debe mata kewa. "Wata uku zaku yi ku dawo hutu, na hada ki da 'yar uwarki Humairah don ki ji dadin zama kina ganin na gida a kusa da ke. Ki maida hankali kiyi karatu, ki kawo min sakamakon da zan yi alfahari da ke, kin ji Sa'adatu?" Ta gyada masa kai "insha Allah zan yi kokari Alan....guburo, nagode, Allah yayi maka fin abinda kayi min". Shi da Fulanin duka suka kalle ta jin abinda ta ce, don basu yi zaton tana da hankalin sanin an yi mata alkhairi ta bi da kyakkayawar addua irin haka ba. Cikin daren Fulani ta kasa barci, ba kewar Sa'ade ta ke ba, damuwar ta na hada Humaira da Sa'ade da za'ayi ne waje daya, ta san Humaira da shegen kinibibi kamar na uwar ta zata iya jan Sa'ade a jiki ta ji sirrin su ta fesawa uwarta. Don haka ta mike daga kwanciyar ta ta sanya hijab kan rigar barcin ta ta nufi dakin Sa'ade. Ta yi dai-dai sai sharar barci take abinta, santala-santalan fararen cinyoyin ta a waje, rigar barcin ta yaye can sama, gashin kanta da Fanna ta wanke mata dazu da shampoo sai sheki yake ga santsi, sai ta ganta exactly like herself when she was twelve years of age, a perfect replica of Bilkisu! Bata taba yi mata cikakken kallo irin na yau ba, kauyancin duk ya fara barin jikin ta, a maganarta kawai zaka ji shi. Ta daddage ta daka mata duka a cinya, Sa'ade ta zabura ta tashi tana sosa wajen tana mutstsikar ido. "Haka kike kwana tsakiyar kwan lantarki sabida baki da hankali ko? Me yasa baki kashe ba?" Sa'ade ta zumburo baki "ni ban san ana kashewa ba" "daga yau duk sanda zaki kwanta ki kashe fitila mai haske ki bar dim, na ga alama ke kidahuma ce" Sa'ade ta kumburo kumatu bata amsa ba. Ta dora kafarta daya bisa gadon ta tsaya akan daya, sannan ta kama kunnenta na dama da kyau ta murde, Sa'ade ta saki tsuwwa don zafi, Fulani tace "idan kika gayawa wani a makarantar ku ko wadda zaku tafi tare ke 'ya ta ce sai na kabari ya fi ki jin dadi a gidannan, kowa ya tambayeki wacece ni a wurin ki ki ce ke 'yar kanwata ce, babar ki ta mutu, kin ji ni ko baki ji ni ba?" Hawaye na fitowa daga idon Sa'ade ta ce "na ji!". Fulani ta sakar mata kunnen, ta juya zata bar dakin. Sai ta tsinkayo muryar Sa'ade cikin rishin kuka. "Amma me yasa kika tsaneni haka? Da har ba kya so a ce ni 'yar ki ce? Kawai saboda ni Babana talakane ba sarki bane?" Wuta ta daukewa Fulani Bilkisu, ta kasa gaba, ta kasa baya. Bata taba zaton yarinyar zata iya yi mata wannan tambayar ba. Sa'ade tayi murmushi mai ciwo ta share hawayen ta da bayan hannun ta..... "Ki nemo min dan uwan mahaifina na Damaturu, tunda kinsan inda ya ke, insha Allahu zan nesanta kaina dake kamar yadda kike so, zan koma wajen sa". Bata bata amsa ba ta fita daga dakin, jikin ta yai matukar sanyi, bata zaci yarinyar nada hankalin gane abubuwa har haka ba, a shekarun ta goma sha biyu, ko ta yi mata bayani bazata gane ba, bata kin mahaifin ta don talaucinsa sai don rashin SO da zafin AUREN DOLE. Tunda itama 'yar talakawa ce futuk! Gaba da baya, inda halacci ashe kuwa bazata manta talauci sabida arzikin gidan aure ba. Da maganganun da Sa'ade ta gasa mata ta kwana a ranar suna gasa mata zuciya. Shi yasa da safe ta ki fitowa balle ta ga tafiyar ta, bata so ta karasa karya mata zuciya, bata shirya karbar ta matsayin 'ya anan kusa ba kuma har abada bata jin zata iya idan ta tuna Hashimu ne Baban ta. Fanna ce ta zo ta tashi Sa'ade ta taimaka mata tayi wanka, ta bata kayan makarantarta ta sanya, tuni an fidda kayan ta zuwa mota. Tun shigar ta gidan kwana ashirin da daya sai yau ta fito ta shaqi fresh air, daga iskar fanka sai ta A/C. Ta na ta wurga ido ko zata ga Fulani, amma ko motsin ta bata ji ba, ta san kuma bata isa ta shigar mata daki ba bisa umarni ba. Duk ta ji ba dadi da abinda bacin rai ya kwashe ta ta gaya mata jiya. Ta san a matsayin ta na uwa, ko me zata yi mata bata cancanci wadannan kalaman daga gare ta ba. Kawai sai ta kama kuka. Jikin ta a sanyaye ta bi bayan Fanna suka fita daga shiyyar Fulani, kuyangin Fulani na ta kallon ta don su har sun manta tana cikin gidan. Da yake safiya ce basu hadu da mutane sosai a hanya ba sai bayi jefi-jefi amma matan gidan da 'ya'yan su ko jikokin su babu ko daya, kowa yana sashen sa. Har suka shiga dalleliyar motar da direba da dogarai biyu ke ciki, daya na tuki, daya na gefen sa. Sa'ade bata bar kuka ba. A jikin motar an rubuta da ruwan gwal "ASKIRA EMIRATE". Gefen hagu dogarawa suka bude mata ta shiga, kafin su rufe kofar ta kamo hannun Fanna, idanunta narai-narai da hawaye tace. "ki ce ma Fulani don Allah don Annabi ta yi hakuri". Fanna bata san akan me ake aiken ta bada hakurin ba, ta dai lura akwai wani babban al'amari tsakanin uwargijiyarta da wannan bakauyiyar yarinyar. An raineta ne kawai a bisa bin umarni, babu tambaya, don haka tace "insha Allahu zan gayawa Fulani sakon ki". Fanna na barin wajen ba da jimawa ba Sa'ade ta hango wata kyakkyawar budurwa na tahowa karkashin rakiyar bayi 'yammata tsararrakin ta, tafiyar ta kawai data banbanta da tasu ya sa ta gane itace Humaira da Alanguburo yace zasu tafi tare wato 'yar autar sarki. Duk da kayan makaranta ne a jikin ta irin wadanda ke jikin ta amma an dora farar alkyabba wadda ta sha aiki da zare ruwan gold mai matukar walwali akai. Tun kafin ta karaso dogarawan nan suka bude kofar da azama suna yi mata kirari irin wanda 'ya'yan gidan kawai ake yi wa. Ta shiga barin dama, yayin da Sa'ade ke barin hagu. Da ta zo bakin motar sai kuyangar dake bayanta ta zare mata alkyabbar ta shiga daga ita sai kayan makaranta. Daga haka aka ja sullubebiyar motar a hankali suka soma tafiya, kuyangin nata basu bar wajen ba har motar su Sa'ade ta hau kwalta. Tunda suka mika hanya sosai yarinyar take ma Sa'ade kallo na kurilla, ita kuwa tun gaisuwar farko data yi mata bata kara ce mata komai ba. Ta maida hankalin ta ga kallon hanya suna wuce bishiyu da dazuzzuka kamar walkiya. Sanda suka cimma garin Chibok ta ce da Sa'ade cikin ginshira. "Me ye hadin ki da Fulani?" Sa'ade ta tuna gargadin Fulani don haka nan da nan tace "ni 'yar kanwar ta ce, mahaifiyata ta mutu". Gimbiya Humaira ta yi mata kallon shakka don ita dai bata taba ganin irin wannan kamar ta kwabo da kwabo ba irin wadda ke tsakanin Fulani Bilkisu da yarinyar da ke gefen ta. Kamar kamannin sun zarta na matsayin data ambata din na kasancewar ta 'yar kanwa a gareta. To amma wace hujja gareta na karyatawa? Tunda ta san bata haifi 'yar a gidan su ba? Sai ta dauke kai itama ta koma kallon gefen titi. A ranta tana fadin ita sam bazata yi mu'amala da 'yar kalen dangi ba mai maganar kauyawa. **** EL-KANEMI COLLEGE OF ISLAMIC THEOLOGY Makarantar kwalejin kimiyya ce ta addinin muslunci wadda Larabawan Yemen dana Sudan suka bude a Maiduguri da hadin gwiwar manyan masu kudin jihar Borno. Itace makarantar da sarki Yusufu ke kai 'ya'yan sa maza da mata, tun daga kan babbar 'yar sa (Ya Maira) sunan sarautar ta kenan a matsayin ta na babbar 'ya, har zuwa kan auta Humairah. A tsarin makarantar daga Lahadi zuwa Alhamis sune renakun karatu, Juma'ah da Asabar renakun hutu. Malamin maths na fita na Qur'an na shiga, na English na fita na Nahawu ko Fiqh zai shiga, na chemistry na fita na Adab ko Tarikh ko Mutala'a zai shiga haka dai tsarin karantarwar su yake. Wato kimiyya cakude da ilmin addini tsantsa. Sannan ana gama lessons karfe uku ake fara Islamiyya ga mai son haddan Qur'an zalla ake yi har zuwa biyar na yamma. Malaman makarantar kuma yawanci larabawan Sudan da Yemen ne, sai kuma Yarabawa Maza da mata basa haduwa sam, dan katanga ce makekiya a tsakanin su sannan kowane bangare da gate din shi. Tunda aka kai Sa'ade da Humairah dormitory dalibai 'yan uwan su ke kallon su, ba don komai ba sai don irin tsadaddun kayan abincin da ake shigo dasu katan-katan ana loda musu a lokokin su, a karshe lokokin nasu ma sun yi kadan su kwashe kayan, sai Humaira ta ce da metron da masu jerawar su je da sauran ta bar musu. Ko kallon Sa'ade bata yi kada a ce tare suke, amma kayan abincin su ba banbanci haka takalmi da jakar makarantar su, wanda ya tabbatarwa 'yan dakin cewa tare suke din. Gadon Humaira na gefen na Sa'ade, don haka ta yi amfani da wannan damar ta maida ita baiwar ta, komai tana daga kwance take sa ta ta yi mata, dauko wannan miko wancan, ko kofi zata yi amfani da shi sai ta sa Sa'ade ta wanke mata shi, kuma da yake Sa'aden ta iya kitso ita ke yi mata duk sati, basa yin wanki iyayensu ke biya a wanke musu shiyasa Sa'ade ta samu sauki, da har wanki da guga ita zata ce ta yi mata. Girman kai irin na Humaira ya hanata alaqa da mutanen dakin, ita kadai take rayuwar ta ko a class don bata ga wanda ya isa tayi mu'amala da shi ba duk da cewa duk 'ya'yan masu kudi ne a makarantar amma a wurin Humaira in ba ka da jinin sarauta cikin jikin ka to baka isa mutum ba. Kuma duk makarantar ita kadai ce 'yar Sarki. Sabanin Sa'ade wadda ta maida kanta abokiyar kowa a dakin nasu, in har bata hidimar Humaira to zaka sameta cikin jama'ar dakin suna hira da harkar arziki, ga ta da kyauta, haka take ta rabar da kayan abincin nata musamman ga wanda ta lura yana da bukata, cakuduwar ta da dalibai 'yan uwan ta wadanda suka fita experience da exposure ya sa ta fara samun wayewar kai. A aji kuwa duk ita ce koma baya a kowane darasi daga na boko har na addini, amma bata barin hakan ya kashe mata gwiwa, ya cire mata hope na cewa da sannu zata iya idan ta sanya jajircewa da bada himma. Haka monitar ajin nasu Raheema Kyari ke yawan gaya mata, wadda tasu ta zo daya, sakamakon yawan tambayar ta abubuwa da Sa'ade ke yi idan bata gane ba ba tareda nuna jin kunya ko girman kai ba. Ba ajin su daya da Humairah ba ita 'yar JSS 3 ce yayin da Sa'ade ke JS 1. Don haka tafi jin dadin rayuwa a class fiye da a dormitory (dakin barcin dalibai) sabida babu Humaira mai takura mata, a nitse take karatun ta tare da likewa monita Raheema tana daukar ilmi daga wajen ta. Malaman ko sun so yin korafi akan rashin kokarin Sa'ade sai su fahimci abin nata daga tushe ne wato bata samu foundation a makaranta mai kyau ba kamar sauran daliban makarantar, don in sun tambayeta wace makaranta tayi tana gaya musu a kauyen Tsanyawa ne, makarantar da maigari yasa aka bude, don a koyawa yara A BA CA DA sai su daga mata kafa musamman in suka lura da yadda take da kishin abun a zuciyarta, in aka koya abu bata gane ba har kuka take yi. Duk kokarin Raheemah na koyar da ita ba komai take ganewa din ba musamman darasin lissafi, da yawa a makarantar sun dauka Sa'ade baiwar Humairah ce, irin 'ya'yan bayi da ake hado 'ya'yan sarakai dasu su zo makaranta tare don su dinga hidimta musu, sabida haka Humairan ke nunawa. Sannu-sannu bata hana zuwa, saidai a dade ba'a je ba, a hankali Kwakwalwar Sa'ade ta soma budewa, musamman a haddar Al'qurani da Ingilishi. Raheema ta taka rawar gani akan hakan don fisabilillah take kaunar Sa'ade sabida saukin kanta, baban Raheema babban dan kasuwa ne a jihar Maiduguri wanda sunan sa yayi fice akan sana'arsa ta fata. Watarana Raheema ta kawo wa Sa'ade ziyara dakin su, sai ta same ta durkushe gaban Humaira ta sunkuyar da kai tana hawaye, Humairan na ta zazzzaga mata fada har tana fadin dama 'yan kalen dangi basu iya cin arziki ba, banda haka tun safe ta sa ta gyaran sittirunta amma tasa kafa ta fice yawon neman suna bata gyara mata ba, su ko Fulani Bilkisu ba wata tsiya bace a wurin su tunda sun san asalin ta balle su ya-ku-bayin data kawo musu gida suna cinye arzikin Babansu. Ba fadan data ke mata ne yasa ta kuka ba, domin in da sabo ta saba, ambaton sunan Fulani data yi ta zaga ne ya tsaya mata a zucci. Ya kona mata zuciya. Fulanin da has never been nice to her in any way amma zuciyar ta na mata wani irin so, da bata taba jin sa akan kowa ba including Baban ta. Rahima ta kama hannun ta ta cira ta tsaye suka bar dakin, Humaira ta sakar musu tsaki tana fadin "ya'yan mutsiyata, gayyar tsiya". Can bayan dormitory suka zaga suka zauna akan duwarwatsun da ke wajen, Raheema ta ce "wai don Allah Humaira ke baiwar ta ce? Ko iyayen ki bayi ne a gidan su?" Bata san me yasa ta yarda da Raheema ba, tun sanda ta fahimci Raheemar na tausaya mata tsakani da Allah. Ta girgiza kai tare da share hawayen idon ta "ni ba baiwar ta bace, ana riko na ne a gidan su, kishiyar mamanta ce yar mahaifiyata a hannun ta nake". Raheema tace "tabdi! Amma shine kike mata bauta tana miki wannan wulakancin? Ke ba baiwar ta ba iyayenki ba bayin su ba? To wallahi ki kama kan ki, ki nuna mata zaman kan ki ke yi ba zaman ta ba in ba haka ba watarana sai ta kai ga taba lafiyar jikin ki" da sauri Sa'ade ta girgiza kai. "Zan yi mata komai saboda Baban ta!". Raheema ta rasa abinda zata ce, sabida a amon muryar ta kadai ta fahimci akwai wani girmamawa da kauna na musamman data ke yi wa Baban Humaira, abinda ta fada har zuciyar ta ya ke. Wannan ya tabbatar mata Sa'adatu irin mutanen nan ne da basa manta alkhairin da wani yayi musu komai kankantar sa. **** An yi jarrabawar karshen zango, as expected Sa'ade ta dauko na biyun karshe, ta yi kuka har ta gode Allah, amma a islamiyya ta yi dan kokari ba laifi musamman a hadda. Damuwar ta yadda zata dauki wannan mummunan sakamako ta kaiwa Alanguburo, bayan ta yi masa alkawarin yin kokari iyakar iyawar ta. Raheema ta ce ta bata lambar wayar wani a gidan su zata kira ta in ta koma gida, Sa'ade tace banda Fulani babu mai waya a sassan su, ita kuma bata san lambar ta ba, ko ta sani bazata yi karambanin bayarwa ba Fulani ta tsinke mata kunne haka kawai. A daren ta hada musu kayan su da zasu tafi dasu gida a kananan trollies din su, sauran kayan abincin da suka rage Humaira tace ta fitar duka ta kaiwa metrons. Ta yi sallama da 'yan dakin su cike da kewa suna fadi a ransu ai gara ta je gida ta huta da wannan bautar data sha ta gimbiya Humaira, wasu kuma suka ce a ran su watakila har a gidan ma irin bautar data ke mata kenan. Kusan su ne na farko da aka zo dauka a washegari. Suna tsaye ita da Raheema a jikin bishiya suna hira, Humaira na daga zaune a gefe akan jijiyar bishiya tana ta harare-harare irin wanda ta saba da kallon kowa a wulakance. Zungureriyar mota kirar 4matic baka wuluk ta yi parking a gefe, da rubutu baro-baro cikin ruwan gwal "ASKIRA EMIRATE". "Ma'assalam Raheema, an zo daukar mu" Ta fada tana jan trollies din biyu dake gaban ta, nata da na Humairah, Raheemah ta daga ido tana kallon inda ta nufa, tun kafin ta karasa dogarawa biyu suka yi wuf suka fito daga motar suka karbi kayan hannun ta. Ta karanta rubutun ta sake karantawa "ASKIRA EMIRATE" Ashe daga masarautar Askira suke, no wonder Humairah take mulkin data ga dama. Baban ta ya sha basu labarin masarautar Askira da irin dimbin arzikin ta da shaharar ta a yankin Borno. Ta karasa da gudu ta cimma Sa'ade, ta rike hanayen ta, tana murmushi ta ce "ki gaida mun Fulani, i will give you a giant surprise insha Allah" Sa'ade ta yi dariya ta ce "Fulani zata ji, ki gaida Mama dasu Sarina (kannen ta)". Raheema na juyawa ta kusa karo da Humairah, da sauri ta bata hanya sabida mugun kallon data sakar mata. Ta shiga gefen dama data saba zama dogarin ya rufe kofar. Ya zaga mazaunin sa ya zauna suka ja motar zuwa get, inda suka cike takardun daukar dalibai sannan aka basu dama suka wuce daga get din makarantar. Tun daga kofar gida kuyangin Humaira na tsaye suna jiran isowar ta. Cikin rakiyar su suka wuce cikin gida kowacce ta doshi bangaren su. Fanna ta fara cin karo da a bakin kofar shiga unguwar Fulani Bilkisu da alama jiran karasowar ta take, tana mata murmushi tace "sannu da zuwa 'yar gida na, yaya hanya kuma yaya karatu?" Tare da karbar jakar kayan ta wadda Humaira ta hana kuyangin ta su daukar mata. Suka wuce zuwa ciki, tsakanin ta da sauran bayin Fulani sai ido, don ba'a basu damar alaqa da juna ba, only Fanna. Ta kaita har dakin ta, ta hada mata ruwan wanka a bathtube sannan ta fita don ta kawo mata abinci. Sa'ade tayi wanka ta ji dadin jikin ta, ta sauya kayan makaranta zuwa doguwar rigar atamfa exclusive mai hasken sararin samaniya, sosai tayi kyau, farar fatar ta ta yi tas, wanka da tsafta sun kama jikin ta, ita kanta data tsaya a jikin mudubin dogon yaro ta kalli kanta sai da ta razana, don gani tayi kuruciya kadai ce zai sa ta kasa cewa Fulani Bilkisu ce a cikin mudubin. Ta ga ta kara tsayi, hancin ta da idon ta sun kara fitowa dara-dara, tsarki ya tabbata ga Ubangijin halitta. Sai data ci abinci ta koshi tayi sallar data kufce mata sannan ta hau gado sai barci. Cikin barcin ta ji an dala mata duka a cinya, ta zabura ta mike zaune, Fulani ce tsaye a kanta ta ci gayu kamar mai shirin gasar sarauniyar kyau. "Wa ya ce da ke ana barci bayan la'asar? Kidahuma kawai". Ta zumburo baki tana mutstsikar ido. "Amma ko sannu da zuwa baki mun ba kin rufe ni da fada, don Allah Fulani me na yi miki ba kya so na?" Ta saki kuka har da na shagwabar ganin uwa, ba wai na zafin fadan da ta yi matan ba. She just felt relaxed by seeing her......after missing her for over ninety days. Fulani ta saki baki tana kallon ta don bata ga abun kuka ba don kawai tace ta daina barci bayan La'asar. Tsaki tayi tace "ba'a son naki, an ki a so ki din, ubanki ya ja miki, banda alfarmar Askirama wallahi bazaki zauna mun a gida ba, Damaturu zan kai ki". Sa'ade ta ida rushewa da kuka, it's painful uwar data haife ka ta bude baki tace bata son ka sabida mahaifin ka komai kazantar laifin uban naka ai mutuwa ma na kunyar idon Da. Balle in ta tuna Uban nata da akewa kiyayyar ba ya duniyar ma. Ita Fulani wace irin zuciya gareta? "Duk talaucin sa dai bazaki kankare cewa shi kika fara aure ba, tun da ga ni.....", sai bayan ta furta kalaman wadanda a zahiri a zuciyar ta tayi niyyar fadar su, ta yi maza ta toshe bakin ta da ta fahimci sun fito fili, amma ina! Already Bilkisu ta ji su. Har ta kai bakin kofa gabadaya ta juyo, ta kankance idanu ta kai mata wani wawan mari, Sa'ade ta kauce amma saida ta samu bayan kunnen ta, dan kunnen ta ya fice ya karce gefen kunnen ta sosai jini ya kwanta a wurin tare da yatsun Fulani Bilkisu. "Wannan ya zamo rana ta karshe da zan kara yin magana ki maida mun, mara kunyar banza! Mai mugun hali irin na uban ta!" Sa'ade na kuka wurjanjan Fulani ta bude kofar dakin ta fice. Tana zuwa falon ta ja ta yi turus! Ganin Askirama a zaune yana jiran fitowar ta. Ya sauke nagartattun idanun sa akanta, ma'abotan kamala da ilhama, a hankali ya ce. "Koma ki kirawo min ita, na jiyo kukan ta". Bata da damar yin musu, haka ta koma jiki a sanyaye tace daga bakin kofa. "Ki zo Askirama na kiran ki". Without giving her a second look ta fice ta bar dakin. Sa'ade saida taje toilet ta wanke idon ta don dai ta boyewa Alanguburo cewa kuka take, amma tana fitowa ta zauna a gaban sa idon sa bai sauka a ko'ina ba sai a bayan kunnen ta. Ya kamo fuskar Sa'ade ya kalli ciwon sosai, yace "Sa'adatu ki yi hakuri kin ji? Ni na gaya miki watarana in wani daban yayi miki haka, sai inda karfin ta ya kare". Sa'ade tayi murmushi duk da idanun ta sun kumbura, a ranta tana tantamar zuwan wannan ranar. Yau ta yarda da gaske Fulani ke kin Baban ta wanda shine mujazar nata kiyayyar. Amma bata ga laifin ta ba, laifin kanta ta gani, da ta ke kasa tankwara zuciyar ta ta mayar mata da magana. Wanda ko kusa bata cancanci hakan daga gareta ba. "Alanguburo ka taya ni bata hakuri don Allah, ni na bata mata rai". Ya yi murmushi ya ce "babu komai ta hakura, amma nan gaba ko me zata yi miki kada ki ji haushin ta, sannan kada ki tanka mata. Uwa ta wuce duk inda kike tsammani. Matsayin ta da darajar ta daban yake dana kowa a wajen ubangiji. Sai da Ya ce abi ta.....a bi ta.....a bita... sau uku kafin ya ce abi Uba. Ina fata kin fahimce ni?" Hawayen nadama na zuba a idanun ta ta gyada masa kai, ta dago ta dubi Fulani da appealing look, amma sai Fulanin ta kauda kai idanun ta jazur, ko kusa bata yi nadamar ciwon data ji mata ba da jinin data fitar mata, ta ma so ya fi haka, tunda ita bata da kunya. Amma can a karkashin zuciyarta ta ji wani sashe daban ya darsa mata tausayin yarinyar. Sanin cewa bata da kowa da zata raba a rayuwar ta sai ita, amma duk kokarin ta ta kasa sanya ta a ranta. Watakila sai ranar da Sa'aden da kanta ta yarda cewa ba laifin ta bane duk abinda take yi mata akan baban nata. Ko kuma ranar da zuciyar ta ta gaji ta russuna ta karbi Sa'aden don kan ta. "Je ki ki huta zan sa a kawo miki magani ki sha". In ji Alanguburo. Har ta mike sai kuma ta dawo gaban sa ta durkusa. "Ka yi hakuri Alan....ban cika alkawarin dana yi maka ba, ban yi kokari a makaranta ba, na yi duk iya kokarin da zan iya amma na kasa kamo kowa....a karshe nice ta biyun karshe". Yana murmushi ya ce "to ai babu komai tunda kin kada mutum daya, a ta gaba na tabbata goma zaki kayar, a ta can gaba ashirin, a ta gabanta talatin, daga haka har ya zamo kece a saman kowa. Kada hakan ya karya miki gwiwa kin ji? Ba wanda aka haifa da iyawa, kowa a hankali yake zama gwani, je ki kwanta ki huta sosai kafin a kawo maganin, ko talbijin ban yarda ki kunna ba sai gobe". Cikin jin dadi ta amsa tareda yi masa godiya, ta saci kallon Fulani ta ga harara kawai take zabga mata, ta wuce su zuwa daki kamar kazar da kwai ya fashewa a ciki. Barcin da ya ce ta yi, ta so ta yi amma ta kasa, duk tunanin ta na yadda zata dinga yiwa Fulani biyayya ne, insha Allahu daga yau bazata sake bata mata rai da gangan ba. ***** "Me ya kai ki? Me ya kai ki dora hannu a jikin marainiyar Allah Bilkisu? In da ya zo da tsautsayi kin kurunta ta fa? Wallahi bar ganin ke kika haife ta, akwai hisabi tsakanin 'ya'ya da iyayen su". "Ku yi hakuri Askirama!". Abinda ta iya furtawa kawai kenan, ya mike cikin bacin rai mai tsanani ya ce "ni kam ba abinda kika yimin sai kyautatawa, balle ki bani hakuri, tunatarwa ce kawai nake miki domin tana amfanar da muminai. Amma tunatarwar da kullum sai an maimaita maka ita, ban ga amfanin ta ba. Daga yau bazan kara yi miki magana akan 'yar ki ba, na tabbata kin fi ni son ta. Saidai bana bayan zulunci, ni shugaba ne mai adalci wanda Allah ya damkawa amanar duk wani talaka da ke cikin garin Askira babba da yaro, balle wanda ke cikin gida na karkashin iyali na don haka bazan lamunci duka ba, in kin so ko dakin ta ki daina shiga wannan ya rage naki, amma duk ranar da kika sake kai hannu a jikin ta zaki ga bacin rai na Bilkisu". Ta tabbatar yau ta kure hakurin mai Askira, dole ta kwantar da kai tayi ta bada hakuri. Tsakanin mace da miji sai Allah balle Bilkisu da Sarki Yusufu mai Askira. Soyayyar su wata ajiya ce daga Allah. Wadda babu irin ta a wannan zamanin, soyayyar mazan jiya masu dattako da sanin yakamata. Fanna ta kawo mata magani ta sha, arashin sanin ta har da maganin barci a ciki. Haka tayi ta barci kuma Fanna bata tashe ta ba saida lokacin sallah yayi. **** Kwanansu bakwai da dawowa hutu, Sarki Yusufu da Fulani Bilkisu da Fulani Hibbani suka tashi zuwa kasa mai tsarki domin gabatar da aikin Hajji na wannan shekarar kamar yadda suka saba duk shekara, yana daukan mata biyu ne cikin matan sa su tafi da kwarkwarori biyu. Harkokin gidan suka cigaba da gudana kamar yadda suke gudana in sarki baya gari karkashin kulawar Wazirin gari Ibrahim. Kadaici ya kara yi wa Sa'ade sallama, bata ganin kowa sai Fanna, bata zuwa koina daga dakin ta sai falon Fulani na karshe wanda babu mai shigar shi in ka dauke Fanna. Ta kagu a koma makaranta ko ta hadu da Raheemar ta su yi ta karatun su ya fiye mata wannan jin dadin mara 'yanci. Domin kafin Fulani ta tafi ta ja kunnen ta sosai akan kowa na gidan koda kuwa bayi ne, bata yarda ko magana ta hada ta da kowa ba sannan bata yarda ko kofar unguwar ta ta fita ba. Ko me take so ta gayawa Fanna zata yi mata. Satin su Fulani biyu a kasa mai tsarki, rannan da Fanna ta kawo mata abincin rana ta hado mata da wata wasika da aka rubuta da fensir, tace "sakon ki ne daga kawar ki". Tun kafin ta bude takardar ta gane rubutun Raheema wadda ta rubuta sunanta a bayan takardar. Raheema Kyari. Jikin ta har rawa yake wajen warware takardar. Ga abinda Rahima ta rubuta. "Hi Sa'adatu, Ni ce Raheema, na zo tun daga Maiduguri as i promised to surprised you, an hana ni ganin ki, don an ce ba'a bada umarnin ki ga kowa ba, sannan Fulani bata gari balle a nemi izninta. Ina fatan ba za kiyi ta kallon talbijin ba, zaki yi ta bitar littatafanki ne kina koyar da kanki kafin mu koma hutu, na so in kwana uku tare da ke don muyi karatu sosai in koya miki mathematics, Allah bai yi ba, musamman Abba ya bada mota aka kawo ni, dana gaya masa masarautar Askira ne bai hana ba. Na so mu hadu, na so in ga Fulani, na so in gan ki, but some other time insha Allah. Mama da Sarina suna gaishe ki. Yours sincerily, Raheemah Kyari. Har hawaye ta yi na bakin cikin rashin ganin Raheema, ta yarda Raheema mai son ta ce, mai kaunar ta ce. Tunda har ta iya biyo ta tun daga Maiduguri har Askira. A karshe ta dauki shawarwarin Raheema, ta daina kunna talbijin, ta mayar da littafanta da darussanta na baya ababen debe mata kewa kuma abokan hirar ta. Sosai take tsintar abubuwa masu muhimmanci, sannan ta dinga tisa haddar ta, Fanna ta kawo mata 'yar radio tana sauraren karatun Abdurrahman Sudaith a ciki. Cikin haka har Allah yayi wa Fulani da maimartaba dawowa daga aikin hajji ana saura kwana biyu su koma makaranta. Suna dawowa shirin komawar su aka fara, aka yo musu provision har fiye dana wancan hutun, babu wanda Fulani bata yiwa tsaraba ba cikin unguwarta (sassan ta). Banda Sa'ade. Ko tsinke bata sayo mata ba. Ita Sa'ade bata san ma an yi rabon tsarabar ba tunda tana cikin daki kullum, ta dai daidaici sanda Fulani take zaman falo ita kadai ta je ta yi mata sannu da zuwa. Tare da tambayar ta "an dawo lafiya?" "Lafiya kalau, alhamdulillahi" Kawai ta ce, ba tare da ta tambayeta komai ba, kamar lafiyar ta ko yadda ta sameta, wannan abu ya sosa ran Sa'ade, ta wuce daki tana share hawaye da bayan hannun ta. Kamar Maimartaba ya san za'ayi haka, da daddare sai ga kyawawan akwatuna manya guda biyu Fanna ta shigo mata dasu, tace tsarabarta ce inji Alanguburo. Ta ce Fanna ta bude mata. Tsala-tsalan dogayen riguna na 'yammatan larabawa ne a ciki kala-kala harda masu ado na sarauta a jikin su, takalma da jakunkuna na yammata masu karshen tsada a daya akwatun kalar kowacce daga cikin dogayen rigunan. Ta cire biyu a ciki ta bawa Fanna, amma sai Fanna tace bazata karba ba Fulani ta basu irin nasu. Wadannan 'ya'yan gidan kawai suke sanya su. Don haka sai ta dauki guda uku a ciki tasa a kayan ta na tafiya makaranta da zummar zata kaiwa Raheemah a matsayin nata tsaraban. Tunda suka dawo hutu wajen kwana arba'in bata kara sa gimbiya Humairah a idanun ta ba, sai yau a cikin mota da zasu koma makaranta. Da ta gaisheta ko amsawa bata yi ba don Fulani Hibbani ta kara ja mata kunne akan mu'amala da ita, ta gaya mata duk abinda Alanguburo ya sayo mata a Saudiyyah irin wanda ya saya mata ne ko banbancin kala babu. Wannan ya kara rura wutar kishin Sa'ade a zuciyar Humairah, ta kudiri aniyar kuntata mata wannan zangon fiye da na baya. **** Da Allah ya tashi taimakon Sa'ade, satin su biyu da komawa aka yiwa dalibai canjin dakunan kwana, inda aka dauke ta daga dakin su Humaira kuma cikin ikon Allah ba'a kaita kowanne hostel ba sai na su Raheema. Murna wajen su abin ba'a cewa komai, a daren ne ta samu ta baiwa Raheema tsarabar data ajiye mata, ita kuma ta bata labarin zuwan ta Askira, tace ta damu baban ta da labarin ta ne ta yi ta rokon sa kan ya sa a kaita, shi kuma ya amince, amma cikin rashin sa'a sai bata samu ganin ta ba. Nan aminci ya kara kulluwa, suka hade kai suka zama kamar 'yan biyu, gasu dama tsayin su daya, sai dai Raheema baka ce sosai cikakkiyar Kanuri, yayin da Sa'ade take jajawur kamar Fulani Bilkisu. Kawancen Sa'ade da Raheema ba karatun Sa'ade kadai ya taimaka ba, ya taimaka mata a sauran fannoni na rayuwar diya mace, tsafta, kwalliya, da iya magana, hatta tafiyar ta Raheema gyara mata take don tace tana tafiya gaba-gadi babu tsanaki. Ta koya mata magana a hankali cikin nutsuwa da yadda zata dinga gyara da kula da sassalkan gashin kanta na Shuwan usli. Rayuwar Sa'ade ta yi ta samun cigaba islamically, educationally, socially and morally a makarantar EL-KANEMI COLLLEGE OF ISLAMIC THEOLOGY. Balle yanzun da bata da tension din Humairah, kowa son ta yake a dakin su, kowa so yake ace shi abokin ta ne. Ga hannun ta a bude, kyauta gare ta kamar 'yar siyasa. Kwakwalwar ta ta bude a lokaci daya kamar kiftawar ido, take grasping ilmi na kowanne bangare wanda nan da nan ya kara canza ta. Dama Alanguburo ya ce mata tunda ta kayar da mutum daya, to nan gaba zata kayar da goma ne, to ba goman kadai ta kayar ba talatin ta kayar, ita ce ta dauki na goma a ajin su, Raheema ta dauki na farko. Don haka da karfin gwiwarta ta dawo gida wannan hutun. Amma har ta kwana ta wuni, bata ga Fulani ba haka bata ji shigowar Alanguburo sassan su ba. Ta gaji da kallon kofar dakin Fulani ta tambayi Fanna, sai Fanna tayi murmushi ta ce. "Fulani ta tafi kasar India zata haihu". Ta rasa a wane yanayi ta karbi zancen, haihuwa? Daman ciki gare ta? Tana farin ciki da jin zata samu karin mutum a kusa da ita, amma wani gefen na zuciyarta yana kishi. Idan ta tuno dama fa Fulani ba wai tana son ta bane, inaga ta samu dan kanta da ta haifa a gidan sarauta? Ai wulakanci gareta zai koma mode activated. Ta kyabe baki tareda cewa "Allah ya sauke ta lafiya". Hutun nasu dama ba mai yawa bane, na sati biyu ne, har sati biyun ta cika Fulani bata sauka ba balle ta dawo, suka koma makaranta zuciyar ta cike da kewar ta, bata san tana son ta har haka ba, sai yau da ta nemi ganin ko inuwar ta cikin gidan ta rasa. Shima Alanguburo Fanna tace yayi tafiya zuwa kasar Amsterdam (Neitherlands) shi da Ya Gumsu kaiwa babban dan Ya Gumsu dake karatu a can ziyara. Rayuwa ta mikawa Sa'adatu Hashim a makarantar EL-KANEMI da budi da nasara da cigaba ta kowanne bangare. Wani sihirtaccen kyau ke bayyanarwa Sa'adatu wadda zuwa yanzu Sa'ade ya bace bat da taimakon Raheema, dama itace in an tambayeta sunanta sai ta ce Sa'ade Hashimu, bayan ba haka yake a rubuce a rijista ba. Raheema ta tsaya tsayin daka wajen tabbatar da ta mantar da ita rayuwar ta ta kauye, ta yi adopting rayuwa mai cike da cigaba, wayewa da aji daidai na shekarun su, kaunar su da juna abin akwai sha'awa da burgewa a ciki. Ranar wani visiting ne Raheema ta kira ta don ta gaisa da 'yan gidan su, fuska fal far'a take gaida Abban Raheema da mamanta, Bakin Babarbare mai zanen bare-bari akan fuskar shi ya sha manyan kaya na kamala, bayan sun gaisa ya sa musu albarka sai ya kasa dauke ido akan Sa'ade yana tunanin inda ya san wannan fuskar. Tabbas ya san fuskar amma ya rasa ta inda ya santan. Yana ta kokari ya tuna amma ya kasa. Har Sa'ade ta yi musu sallama ta koma cikin dalibai 'yan uwan ta. Su dama ba'a zuwa musu visiting daga ita har Humairah, aiken kayan abinci kawai ake musu daga gida a kowanne visiting. Amma yau tana tsaye cikin daliban da ba'a zo musu ba ta hango shigowar motar data bata mamaki, bakar 'Land Cruiser' ce mai tsayi dauke da rubutun 'Biu Emirate'. Ba ta tafi wajen motar ba ta tsaya a inda take tana kallon su, don ta san ba wajen ta aka zo ba sai dai ko Humairah. Wasu hamshaqan 'young ladies' ke fitowa daga motar tare da kyawawan 'ya'yan su kanana maza da mata, matan su hudu ne, daga inda take tsaye ta hango Humaira ta nufo su, duk jan ajin ta yau sai da ta hada da gudu-gudu ta rungume babbar cikin su. "Yaa Maira! Ashe da gaske zaku zo?" Ya Maira itace babbar 'yar sarki Yusufu, sunan sarautar ta kenan 'YaMaira' a matsayin ta na babbar 'ya. Sai mai bi mata a dakin Ya Kirjinoma wato Mairam Murjanatu, sai kanwar Murjanatun Mairam Naja'atu 'yar Hibbani, wadda Humaira ke bi a haihuwa. Ya Maira tana aure ne a masarautar Biu yayin da Murjanatu ke auren Ambasadan Najeriya a Turkiya, ta zo ganin gida ne tareda 'ya'yan ta ta tadda Ya Maira ta zo daukar Naja'atu su zo wa auta ziyara kamar yadda ta alqawarta mata, sai ta biyo su, don itama ta jima bata ga Humairan ba. Wani kilishi mai taushi baiwar da suke tare ta shimfida musu, ta koma motar ta soma fiddo sundukan abinci na alfarma da picnic coolers masu dauke da ababen sha masu sanyi. Nan suka baje suna ta hira, kai bazaka ce 'ya'yan kishiyoyi bane sabida shaquwa da kaunar da ke tsakanin su sabanin iyayen su da ke zaman kishin kwatar kai. Naja'atu ta juya idanun ta kan Humaira, "Hummy ina yarinyar da ake kawo ku tare ne 'yar kalen dangin da kike cewa? Kin ji uwar rikon nata ta haihu ko?" Humaira tace "wai wannan 'yar mutsiyatan nan, ni rabon da insa ta a idona tun ranar da muka dawo hutu, da yake an raba mana daki". "Wace yarinya kuke magana ne? Menene kuma kalen dangi?" Inji Mairam Murjanatu. (Mairam title ne na kowacce 'yar sarki). Humaira ta ce "yarinyar da Fulani Bilkisu ta dauko riko, da fari cin uban ta nake yi as if na samu baiwa, sai kuma aka zo aka raba mana daki aka barni da cizon yatsa". Murjanatu tace "dadi na da ke Humaira baki da kirki, albarkacin zaman tare ai ko gaisawa kya dinga yi da ita, ni na rasa inda kika dauko wannan fadin ran naki, na san dai ba daga Fulani Hibbani ba haka ba daga Alanguburo ba". Dama can Murjanatu tafi kowa saukin kai cikin 'ya'yan sarki kai bazaka ce ita 'yar gidan bace. An raine su akan yiwa wanda ke sama da su biyayya! Wannan ne ya sa Humaira ta kira wata junior din ta tace ta je ta zo mata da Sa'adatu Hashim. Ya Maira bata ce musu komai ba. Sai dai itama tana son ganin 'yar da Fulani Bilkisu ke rikon. Suna tsaye itada wata 'yar ajin su Falmata wadda itama ba'azo mata ba, yarinyar da aka aiko ta zo ta same su, tayi mata nuni da inda suke zaune tace "ki je in ji Princess Humaira". Saida ta ji gabanta ya fadi don ita har ta manta da matsalar Humaira, tace da Falmata "ina zuwa" sannan a hankali ta soma taku cikin nutsuwa zuwa inda suke zaune. Tunda ta doso su taji gabanta na faduwa, duka fuskokin bata san su a gidan ba banda Humaira amma ta gane iyalin Sarki ne. Haka suma suka zubo mata ido cikin tsananin mamaki a fuskokin su, hatta gait (takun tafiyar ta) irin na Bilkisun Askirama ne. Is it possible dan kanwarka yayi irin wannan kamar da kai har fiye da dan da za'a ce kai ka haifa? Har ta tsugunna ta soma gaishe su an rasa mai magana a cikin su, sai kallon ta suke with astonishment, duk sun mata kwarjini irin na su na 'ya'yan Saraki ta kasa ko duban fuskokin su. Ya Maira....ji tayi zuciyar ta na bugawa, tana da wata baiwa ta sunsunar kaddara. Haka kawai jikin ta ya bata akwai wani babban al'amari da zai zo ya kasance tsakanin su da yarinyar nan wanda bazata ce menene ko na menene ba. So she became mute, kamar an dinke mata baki, ko gaisuwar Sa'ade bata iya ta amsa ba. Murjanatu ce ta kawar da mamakin ta ta amsa mata gaisuwa, sannan ta ce Yaya karatu? Ina fatan kina kokari? Kuma kina jin dadin makarantar taku?" Sa'ade tayi murmushin da ya fidda beauty point a barin hagu tace "ina yi ranki ya dade, kuma ina jin dadin makaranta" tana ta kallon yaransu cikin sha'awa kasancewar Allah ya sanya mata son yara kamar me, Murjanatu ta nunawa baiwar da suke tare daya daga kulolin abincin da suka zo da su tace ta dauka ta bita da shi har kofar hostel. Sa'ade tayi ta godiya, ba don yunwa take ji ba sai don karamcin Mairam Murjanatu, a ranta tana fadin ashe akwai mai kirki irin Askirama cikin 'ya'yan sa, at the same time tana ta karbar sakon harara mai zafi daga Humaira. Har ta kule basu daina kallon bayan ta ba, Murja ta ce "Allah mai iko, dole Fulani Bilkisu ta dauko yarinyar nan daga cikin dangin ta, ku dubi kama don Allah har zuba take" Humaira ta kyabe baki ta ce "Ya Murja yanzu ne ta kile fa, da in kin gan ta ko kin ji maganar ta ko kin ga yadda take tafiya sai kin kusa yin amai. Kawaye take bi kamar mayya suna kilar da ita, banda haka bazaki so ki ganta sanda aka kawo ta makarantar nan ba". Murjanatu tace "to ai sun taimaketa, yanzu wannan yarinyar ina ne baza'a shiga da ita ba ko wanene ba za'a iya aurawa ba? Kin ce Alanguburo na son ta, ki zuba ido ki ga irin mijin da zai zabo mata, kin san shi dai da so wa 'ya'yan sa da 'ya'yan rikon sa babban gida". Kishi ya kara turnike Humaira tace "insha Allahu tsohon hakimi zai bata gidan kishiyoyi goma taci uban ta". Ya Maira tace "ka so wa dan uwanka abinda kake so wa kan ka". Haka suka maida Sa'ade da uwar ta topic of discussion har lokacin tafiyar su. A cikin hirar tasu naji Murjantu na gayawa Humaira Fulani Bilkisu ta haihu 'ya mace, amma bakwaini, 'yar tana cikin incubator har yanzu acan kasar India basu dawo ba. Ya Maira tace "dama Alanguburo ya daina asarar kudin sa, sunan wannan din ma matacciya, wadanda ta haifa lafiya ma basu zauna ba balle bakwaini mai cutar sikila. Raheema ta shigo da nata kabakin abincin, nan ta ga abincin alfarmar dake gaban Sa'adatu, tace "yanzu dama 'yan gidanku sun zo shine baki kira ni ba?" Sa'ade ta girgiza kai "ba waje na suka zo ba, ni ban san su bama, arzikin Humaira na ci suka bani wannan din". Nan suka zauna suka soma dibar garar dadin su. Yau kam sun wuni cikin farin ciki marar misaltuwa. A haka zangon karatun ya kare, akayi hutu suka dawo gida. Wannan karon ma bata tadda Fulani a gida ba, Fanna dai ta ce mata ta haihu, bata dawo bane don 'yar bata isa haihuwa ba aka haifeta sai ta yi kwari tukunna a asibiti. Ta kasance cike da farin cikin jin labarin haihuwar nan, ashe itama zata samu dan uwa a duniya, wanda zata kira "kanin ta". Babban abun farin cikin ma diya mace. Sai dai damuwa ta biyo bayan farin cikin da Fanna tace 'yar mawuyaci ne ta rayu. Sai ta ji tausayin Fulani, yadda ta lura Alanguburo na son ta, sai take musu fatan samun rayayyen Da a tsakanin su. Da tayi sallah sai ta samu kanta da daga hannu tana addu'a. "Ya Allah ka raya abinda Fulani ta haifa". Haka tayi wannan hutun ma cikin kadaici da kewar Fulani, amma da yake yanzu ta auri littafan ta sai komai ya zo mata da sauki. Tana son karanta littafan hikaya na turanci, duk da turancin nata baida karfin fahimtar kowacce kalma, sai take yi tana duba kamus na hausa da turanci, haka ta karbo su kala-kala daga library ta taho dasu gida musamman na ZAYNAB ALKALI da ABUBAKAR GIMBA. A wannan hutun saida Sa'ade ta maida kanta 'yar karamar Farfesa a Ingilishi sabida karatu da duba dictionary. Kullum Fanna ta shigo kawo mata abinci abinda zata tarar tana yi kenan. Har ce mata take "ki dinga ajiyewa kina hutawa kada kan ki yayi ciwo". Sai tace da Fanna "da haka ne zan kayar da kowa Fanna, idan na iya turanci, idan ka iya shi kowanne darasi zai zo maka da sauki". Fanna sai tace "to ALLAH ya bada sa'a". Har suka koma makaranta Fulani bata dawo ba. In ka lissafa zaka ga cewa watanni masu yawa kenan basu ga juna ba, wanda hakan ya sanya matukar kewar junan su a zukatan su. Ga Fulani, ba damuwa tayi ta ganta ba don ta san tana lafiya amma somehow tana jin kewar ta a can kasan zuciyar ta. Saidai hankalin ta ya dauku ga son rayuwar abinda ta haifa wadda ke tsakanin rayuwa da mutuwa, don haka bata cikin kwanciyar hankali ko kankani. Shi kam Alanguburo ya gama fidda rai da rayuwar yarinyar kamar sauran wadanda suka gabata. Amma bai fasa karfafawa Fulani gwiwa ba kan tayi hakuri ta barwa Allah ikon sa. Da sun haihu ko basu haihu ba, soyayyar da yake yi mata bazata taba raguwa ba, sannan ba ga Sa'adatu Allah ya basu ba?" Bata cewa komai idan ya fadi hakan, amma a ranta cewa take "yar Hashimu ce ba tawa ba, da sannu Allah zai bar min tawa". A sannu kuma sai Allah ya soma baiwa 'yar koshin lafiya sabida tsananin kulawar data ke samu daga likitoci da adduar uwa, tayi bul-bul kamar ba bakwaini ba, amma still sikila ce. Sun dawo gida ranar wata Lahadi, sati biyu da komawar Sa'ade makaranta. Nan aka yi ta shigowa Fulani barka kamar za'a tsaga sassanta don yawan al'umma, kishiyoyin ta dake jiran gumbar sadaka dole suma suka yi lullubi suka zo barka don ganewa idon su abinda ta haifo ba don barkar ta Allah da annabi bace, "yarinya kamar Murjanatu" inji Ya Kirjinoma cikin al'ajabi. Hibbani tace "wannan dan gajeren hancin ai na Ya Maira ne, Murjanatu mai dogon hanci zaki hada da wannan burtuntunar, ai komai nata na Ya Maira ne" Ya Kirjinoma tace "in zaki tsoraci Allah, Murjanatu ce sak wannan". Fulani tayi murmushi bata ce komai ba, amma burtuntuna da aka kira 'yar ta ya sosa mata rai. Ta san kadan da aikin Hibbani, in ta kwabo maka magana ko zaka mutu ita babu ruwan ta. Amma abin mamaki Ya Gumsu bata shigo ba, tana can bakin ciki na neman kashe ta, don bata taba zaton 'yar zata rayu ba. Haka 'ya'yan gidan maza da mata na nesa dana kusa suka yi ta tururuwar zuwa barka har wajen kwanaki talatin mutane basu tsagaita ba. Daki guda sai da ya cika taf da kayan barka na uwar dana 'yar mai suna "Zarah" Cikin kuyangin Fulani aka warewa Zarah masu kula da ita su biyu, dattijuwa da budurwa, dakin Zarah yana jikin na Fulani, yayin da na Sa'ade ke kallon nasu. Suka cigaba da rainon ta cikin tsananin kulawa. ***** Kayan su suke hadawa itada Raheema kasancewar gobe hutu, suna yi suna hira, Sa'adatu tace "wannan hutun ina duban hanyar ki, na san daga Fulani har Alanguburo in suna gida, baza'a hanaki shigowa ba". "To Allah yasa Abba ya barni, ya ce min ma shi kallon sani yake miki" Sa'ade tayi dariya, "ba dole yayimin kallon sani ba tunda nima 'yar sa ce?" Haka suka yi ta hira har suka kammala hada duk abinda suke bukatar zuwa dashi gida. **** Yarinyar dake tsaye yau a gaban ta wata siririyar budurwa ce, cikin shekaru na tashen balagar diya mace. In bata manta ba tana kamar girman ta aka yi mata auren fari, auren dolen da ya zamo silar zuwan ta duniya. Tana tsaye daga bakin kofa sanye cikin uniform din ta na makarantar sakandire, kyakkyawar fuskar ta kunshe da sassanyan murmushi, wanda kai tsaye ta fassara shi da murmushin farin cikin abinda yarinyar ta shigo ta tarar tana yi (breastfeeding her baby). Ta tako a hankali cikin tafiyar data banbanta da ta SA'ADEN da ta sani watannin baya, mai tafiya tana hada hanya, wannan Sa'adatun a nitse take tafiya. Her gait, her serene smiles duka suna kara tabbatar mata da cewa, ta fito ne daga cikin mahaifar ta kwatankwacin diyar dake rungume a hannun ta a yanzu, wato Zarah. Banbancin dake a tsakani shine; wannan soyayyah ce ta kaita ga haifar ta, yayin da waccan kiyayya ce silar nata zuwan duniya. Ta yi nisa a wannan tunanin har bata san lokacin da Sa'ade ta karaso gareta ba, kokari take ta karbi 'yar daga hannun ta wadda ta saki nono tana kallon Sa'aden da kyawawan idanun ta. Sa'ade blushing ta ke from ear to ear, ta dauka Fulani zata hana ta daukar diyar ta, amma ga madaukakin mamakin ta sai ta ga ta sakar mata. Ta dauki kanwar tata tana ta murmushi. "Beautiful!" Ta fada cike da kauna. Fulani ta cigaba da bin ta da kallo ba tare da ta sani ba, duk wani kankanin canji dake tare da Sa'aden a watannin data kwashe bata ganta ba saida ta zaqulo shi cikin idanun ta. "Ashe kilewar diya mace ba wuya muddin zata je makaranta!" Fulani Bilkisu ta fada a zuciyar ta. Tana son comparing soyayyar data ke ji akan Sa'ade da Zarah. Sai ta ga cewa ratar dake a tsakani mai tsananin fadi da girma ce, ta haifi Sa'ade ne kawai amma babu ko digon soyayyar ta a zuciyar ta, sai tausayi da kyautayi irin na zuciyar musulunci. Yanzu ne ta san kaunar uwa akan dan ta, da ta haifi 'ya da wanda take so. Can wani lungu na zuciyarta kuwa kururuwa yake yana objecting: idan soyayyar Sa'ade da ta Zarah, bata zo daidai da juna ba, sai dai ace ta Zarah ta rinjayi ta Sa'ade, amma ba wai ace babu burbushin ta ko kankani a zuciyar ta ba. Bata ankara ba sai ganin 'yar ta tayi a bayan Sa'ade, tasa tawul din da aka nannade ta a ciki tagoye ta tsam ajikin ta, ta soma dan jijjigata sabida dan rikici data ke yi irin na jarirai. Sai tasamu kanta da kasa cewa ta sauko mata 'yar ta, ta mike ta shige turakarta ba tare da ta ce da ita komai ba. Dama kuma tana so ta huta din, gashi ta sallami kowa tace bata son ganin kowacce baiwa a bangaren ta sai gobe da safe in Allah ya kai mu. Sai ganin tsayuwar Sa'ade ta yi a gaban ta ba zaton ta ba tsammani. Sa'ade saboda jin dadin Fulani ta bar mata Zarah sai ta nufi dakin ta goye da ita, roba ta samu ta hada ruwan dumi ta saukota ta soma yi mata wanka, ta gama ta nade ta cikin shawul ta fito kan gadon ta ta dauki basilin din ta tana shafa mata. A lokacin Fulani ta shigo, ta bude baki da zummar yin fadan don me ta yi mata wanka bayan ba'a jima da yi mata wanka ba? Amma sai ta ga yarinyar na ta bangala dariya Sa'ade kuma ta himmatu wajen yi mata wasa a cute kumatunta. Sai suka bata sha'awa, ta juya silently ta fita. Ta dauko set din kayan baby na sanyi ta dawo ta watsawa Sa'aden ta sake juyawa ta koma. Shikenan daga wannan ranar Sa'ade ta kwace rainon Zarah daga hannun Fulani da masu rainon ta, kayan yarinyar ma saida ta san yadda tayi suka dawo dakin ta. Tsakanin ta da Fulani shine kawai idan ta bukaci nono. Hausawa suka ce wai "Mai Da wawa ne", wannan kyautatawa da kauna ta Sa'ade ga Zarah a hankali yake hakurkurtar da zuciyar Fulani Bilkisu, daga mummunan kullacin Mal. Hashimu dake cikin ta, wanda ya hanata ganin farin Sa'ade har ta kaunace ta matsayin 'ya 100%. A hankali ta soma rage fada, da tsawa da hantarar da take yawan yi mata, ta soma yi mata magana jefe-jefi cikin sanyin rai. Satin ta uku a gida sai ga Raheema Kyari, wannan karon ba'a hanata shigowa ba, Kuyangar data rako ta sai ta hada ta da Fanna, ita kuma Fanna tace ta jira daga waje, ta nemo izni tukunna. "Kawa kuma daga Maiduguri?" Fulani ta fada cikin mamaki. "Haka ne ranki ya dade, sannan ta tabbatar min ita aminiya ce ga Sa'adatu sannan ta san da zuwan ta". Fulani ta hadiye fushin ta wanda tayi aniyar saukewa akan Sa'ade bayan tafiyar bakuwar, ta ce Fanna ta shigo mata da yarinyar. Cikin sallama da shiga ta mutunci da kamala Raheemah ta shigo, tunda ta shigo Fulani ta kura mata ido. She looks so much like her father wanda ta yi wa farin sani. Mikewa tsaye tayi ba tareda ta san lokacin da ta yi hakan ba, hatta tsagin fuskarsa biyu-biyu dogaye gasu nan kwance a fuskar Raheema. Da ta gaisheta da kyar tayi controlling razanar ta ta amsa, "yaya sunanki?" "Raheema Kyari Babagana" "Kyari?!" Ta fada da amon muryar da ya baiwa Raheema mamaki, "eh, sunan Babana kenan" "daga wane gari kike?" "Daga Maiduguri na zo, acan muke zaune, amma mu 'yan asalin Damaturu ne". "Shikenan dangin ubanta sun biyo ta, a lokacin da na fara sanyata a raina". Fulani ta ayyana a zuciyar ta, ta kuma kudiri aniyar kin gayawa Sa'ade kowacece Raheema a gareta. "Shiga nan dakin, tana ciki" Ta fada tare da nuna mata dakin, ta kuma tashi ta bar musu area din gabadaya zuwa turakar ta. Sa'ade sai ganin Raheema ta yi ta shigo da sallama, zo ki ga gudu da murna wajen Sa'ade, saura kadan ta kada Raheema. Ita kuwa sai dariya take. Ta dauki Zarah dake tsakiyar gadon ta tana fadin "masha Allah, beautiful baby". Hira kamar ta kashe su. Fanna ta shigo wa da Raheema abinci na musamman suka ci tare cike da farin ciki. Can da yamma Raheema ta ce "Sa'adatu ki zagaya da ni mana in ga masarautar taku in samu abun baiwa su Sarina labari". Sa'ade tayi dan jimm! Kafin tace "ni bana zuwa ko'ina, daga daki sai daki, Fulani bata bari na". "Amma meyasa?" Inji Raheema. Ta dan kyabe baki "i don't know. May be sabida kishiyoyin ta". Daga haka suka bar hirar. Washegari Fulani ta sa aka yiwa Raheema sallama ta girma, aka maida ita har Maiduguri. **** Ya Gumsu ta shiga turakar mai Askira cikin kwalliya ta kasaita a matsayin ta na mai girki ranar, abinci yake ci tana gefen sa tana masa firfita, cikin hila irin ta matan da suka san kan mazan su ta yi durkuso a gaban sarki, ta ce "Alanguburo (Allah ya kara yawan rai) Yarima na rokon alfarmar a bar shi ya zo gida, ko da na sati daya ne, shekaru goma kenan rabon sa da gida, yayi digiri yayi masta ya jima yana aiki har ya fara digiri na uku, yana cikin damuwar rashin sanin halin da 'yan uwan sa ke ciki, yayi alkawarin baza'a sake samun sa da laifi makamancin na baya ba". Nan da nan wani kwantaccen bacin rai ya bayyana a fuskar sarki, ya dago idanun sa da suka kada ya dube ta, sai da hantar cikin ta ta kada. Ta yi azamar sunkuyar da kai amma a ranta zata jure komai in har zai bar dan ta ya zo gare ta, haka kawai ai ba shikadai ne fitinannen Da ba, fitinannun nawa ya haifa? Amma bai daukewa Ya Kirjinoma nata ba sai shi kadai bayan ba fin su fitinar yayi ba. Yana kusa da su ma suna masa fada ai zai fi gyarawa fiye da hannun aminin nasa. Sarki Yusufu AbdulHakimu mai Askira, ya dubi uwargidan sa Ya Gumsu da idanun bacin rai kamar koyaushe ta sako zancen YARIMA SAGEER a gaban sa, idan da abunda ya ke bata masa rai a rayuwar sa to al'amarin Yarima Sageer ne, babban Da, kuma zakka a cikin 'ya'ya mazan da Allah ya bashi, yet mafi madaukakiyar soyayya a zuciyar sa. Dama an ce wai fitinannun 'ya'ya sun fi shiga zuciyar iyaye. Kusan wannan magana haka take. Duk cikin 'ya'yan sa maza da mata ba wanda yake so irin Muhammad Sageer, sai kuma ya zamo mafi munin jarraba da Allah ya taba yi masa. Ubangiji yayi gaskiya da ya ce "ya'ya da dukiya fitina ne......". "A takaice dai kina rokawa dan ki alfarmar ya dawo cikin gidan nan ya cigaba da turmushe 'ya'yan mutane, ya cigaba da wulakantani tare da tozartani a idanun Bayi na da hadimai na dake tsananin ganin girma na, ta hanyar turmushe musu 'ya'ya dake hidimta masa?". Fulani ta runtse ido cikin jin zafin kalaman sa, "Alanguburo, wannan abu ne na kuruciya, kai kan ka da ka ga Yarima ka ga nutsuwa da hankali a tattare da shi, abinda yayi yana yaro ba zai taba maimaitashi cikin hankalin sa ba, balle da 'ya'yan bayi makaskanta a gare shi. Wallahi don an ki yarda da nine, amma Yarima makiya ne suke jifan sa a baya, ba yin kansa bane. Kai shaida ne akan tsantsani da tsafta irin na Yarima, amma a ce ya rasa matan da zai bi sai 'ya'yan bayi, ai daga nan zaka gane akwai lauje cikin nadi a al'amarin sa. Bayan haka kuma na dukufa da yi masa addu'a tun tafiyar sa, Allah kuma baya juya addu'ar Uwa, inada kyakkyawan yaqinin cewa ya daina, mu taru mu kyautata masa zato, mu bashi dama ya rayu cikin gidan su kamar kowanne Da cikin gidannan, idan aka sake samun sa da wani laifi makamancin wannan, na amince ayi masa duk hukuncin da ya kamata da shi". Maganganunta ga dukkan alamu sun dan shigi Askirama. Ya dade cikin halin shiru, ya kasa cigaba da cin abincin sa. A karshe yace da Ya Gumsu wadda ke jiran amsar sa kamar ta shiga zuciyarsa taga abinda yake yankewa. "Zan yi shawara da Waziri". "Alanguburo (Allah ya kara maka yawan rai nagode matuka, kuma insha Allahu Waziri zai amince da abinda na zo da shi, don shima na tabbata yana son ganin Awaisu)". "Ina bukatar kadaicewa". Ya ce da ita. Ta mike cikin azama ta soma tattare akusan abincin dake gaban sa. "In ma kwana zaka yi kai kadai ka yi, ni dai a bar Da na ya dawo gida". Ya Gumsu ta fada cikin ranta, a fili kuwa dukawa ta yi a gaban sa tana fadin. "Na bar ku lafiya gatan Askira". Fitar ta ke da wuya ya kishingida ya lula cikin tunani. Tunani mai zurfi na shekarun da suka gabata. **** SHEKARUN CAN BAYA (A Masarautar Askira) Lokacin da Ya Gumsu ta samu cikin babbar 'yar sa 'Yaa Maira' duk burin sa da dokin sa shine a haife masa Da namiji domin ya samu magaji, kamar yadda kowanne sarki ke burin samu. Amma sai aka haifi Ya Maira, ciki na biyu ma yayi ta fata da addu'ar samun da namiji, amma sai ta kara haihuwar diya mace. Dalilin sa kenan na kara auren Ya Kirjinoma a daidai lokacin domin yana ganin 'ya'ya mata kawai Ya Gumsu zata yi ta haifar masa. Kamar Allah ya san cewa bai yi farin ciki da haihuwar Mairam Lubabatu ba, bata fi shekaru uku ba Allah ya karbi abinsa. Ya Kirjinoman ma da ta tashi haihuwar ta ta fari, sai ta haifo masa Mairam Murjanatu. Wannan ya kara mayar da shi desperate ga son haihuwar da namiji. Ba ruwan sa da 'ya'yan sa mata, duk kulawar su da hidimar su da tarbiyyar su tana wuyan iyayen su mata. A kullum ya tuna wancan lokacin ya kan ce "wannan shine deadly mistake da ya taba yi a rayuwar sa". Ba shikadai ba, masu sarauta da yawa hakane tunanin su akan haihuwar fari, idanunsu rufewa yake ga son haihuwar da namiji ba tare da baiwa Allah zabi ba. Ciki na uku da Ya Gumsu ta samu kusan a tare suka sameshi itada Ya Kirjinoma. Ita ta haifi MUHAMMAD SAGHEER, Ya Kirjinoma ta haifi MUHAMMAD ASHGAR tsiran watanni biyu kacal ne a tsakanin su. Ashgar sai ya zo da rashin lafiya ta Autism wadda aka fi sani da (autism spectrum disorder). Baya magana (in a meaningful way) tun yana karami saidai ya maimaita abinda aka fada masa sannan kamar kwakwalwarsa ba daidai take ba. Wannan yasa sarki Yusufu ya dauki soyayyar duniya da tattali da kulawa ta duniya bakidaya ya dora akan lafiyayye Yarima Sageer, wanda hakan ya ruruta wutar mummunan kishi tsakanin Ya Kirjinoma da Ya Gumsu, ya kuma sa Ya Gumsu daukar girman kan duniya ta dorawa kanta, da jin tafi kowa, tunda kuwa ita ta haifarwa sarki Yarima. Koma waye zai biyo baya saidai ya zo a matsayin kanin sa ba Yayansa ba. Soyayyar data sa tun yana yaro daga uwar har uban suka sangarta shi, basa iya kwabar sa, gata na duniya babu irin wanda basa gwada masa. Hakan bai hana shi yiwa Sageer addu'a ba a duk sallahr farillar sa kan Allah ya kare masa shi a duk inda ya shiga. Musamman da ya bayyana ga kowa cewa yaron fitinanne ne na kin karawa. Ya addabi 'ya'yan jama'ar gari da mugunta da tsokana, baya zama cikin masarauta saidai cikin 'ya'yan talakawan gari, sune abokan sa abokan mu'amalar sa, don Sageer ya tare yaro a lungu ya targadashi ya fasa masa hanci babu gaira babu dalili ba wani abu bane sabo a wajen jama'ar gari, suna dauke ido ne sabida mutuncin mahaifin sa da farin jinin yaron. Yaro ne mai shiga rai matuka, sabida kwarjini da kyawun suffar da Allah ya bashi. Yana girma fitinar sa na karuwa a ciki da wajen masarauta. Kullum Sageer ya fita makaranta da yaron da zai targada ko ya fasawa hanci ba'a kuma isa a kawo kara ba sabida tsoron Ya Gumsu, saidai Awaisu ya gani ya zo ya fada a gida. Waziri ya aika a bada hakuri. Don ba'a bari ma Sarki ya ji. (Awaisu dan Waziri ne kuma sa'an Sageer don haka tare aka raine su), har ta kai ga Awaisu ya kwaso kayan sa duka ya dawo dakin Sageer kwatakwata, sai dai hali kowa nasa daban. Don kuwa Awaisu babu ruwan shi yaron kirki ne, amma duk inda Sageer yasa kafa nan zai mayar da tasa. Darajar Sarki yasa jama'ar gari suka yi ta hakuri da Sageer tun yana yaro har ya shiga sakandire anan Askira. Kafin ya gama sakandire ne kuma yayi dan hankali ya daina taba 'ya'yan kowa, sabida yawan addua'ar Alanguburo akan sa. Har yake dan shigowa fada a zauna zaman fada tare da shi kamar yadda Sarki ke so ya dinga yi kullum amma ya ki. Lokacin da Sageer ya soma balaga, sai abubuwan gabadaya suka canza, 'yar nutsuwar da yake da ita tabi ruwa. Ya koma neman bayin sa mata. Lokacin da wannan mummunan labari ya kai kunnnen sarki Yusufu mai Askira sai ya kira Wazirin sa cikin sirri. "Na yanke shawarar in aura masa mata hudu a rana daya, ina ganin hakan ne kawai mafita ga al'amarin sa". Waziri Ibrahim ya girgiza kai yana kallon maimartaba sarkin Askira cikin tausayi, ganin yadda ya zabge ya birkice a kwanaki uku kacal da samun wannan labari da yayi. Lallai 'ya'ya da dukiya fitina ne. Kamar yadda mulkin kansa fitina ne da rashin kwanciyar hankali ga bawa. Yace. "Baza'a yi haka ba Askirama. Baza'a yi haka ba gatan Askira, aure ba laifi bane a shekaru goma sha tara amma karatu za'a kai shi, zamani ya canza, auren mata hudu a rana daya ba zai zamo solution ba, don kuwa zai hanashi maida kai ya yi karatu musamman idan ya soma tara iyali. Ka manta da komai ka kwantar da hankalin ka ka barshi yayi karatun da zai amfane shi muma watarana ya amfane mu. Zan hada shi da Awaisu zuwa duk inda zaka kai shi zan kuma san yadda zan yi Awaisu ya zame masa jagora a komai nasa. Mafi a'ala shine mu bisu da addua". Ya sani duk duniya babu mai kaunarsa cikin 'yan uwan sa na jini irin Waziri Ibrahim, wanda ya kasance Da ga wan mahaifin sa marigayi sarki AbdulHakimu mai Askira. Bai taba bashi shawarar da in ya bi ta baya ganin mafita da yaqini a cikin ta. Don haka yayi na'am da shawarar Waziri ba tareda shawara da Ya Gumsu ba. Kafin ya zama sarki shi Ambasada ne na kasar Egypt, saida mahaifinsa Sarki Abdulhakim ya rasu ne aka dawo dashi gida aka bashi sarauta, don haka yana da kyakkyawar alaqa da ambasadan Egypt mai ci a lokacin kamar amini yake a gare shi, sannan yana da connections mai yawa da kasar ta Misra domin yayi sama da shekaru goma yana aikin jakada a cikin ta. Don haka ya yanke shawarar kai shi kasar muslunci bai kai shi kasar turai ba don ya kara hankali, a Egypt din ma hannun Aminin sa Amb. Hassan Labaran ya damka shi bai yarda ya zauna a hostel ba. Amb. Hasan bai taba haihuwa ba shida matarsa Hajiya Laila, suka karbi amanar Sageer da Awaisu a gidan su wadanda aka samarwa gurbi a jami'ar Al. Azhar. Saidai ba fanni daya suke karanta ba. Daga wannan lokacin ne kuma haihuwar 'ya'ya maza ta budewa Sarki Yusufu daga duka matan nashi biyu, a lokacin ne ya hadu da Hibbani ya aure ta, daga baya ya auri Bilkisu, haihuwar ta biyar suna mutuwa. Amb. Hassan zazzafan da boko ne mai zafi da sanya ido akan iyalin sa, tashin farko ya gano dabi'ar da Sageer ya zo masa gida da ita ta shan sigari, kuma ba jimawa yayi fata-fata da ita, ya cigaba da dora shi a hanya ta hanyar tsawatarwa da jan sa a jiki, yana nuna masa illar smoking ga lafiyar sa ta dan adam. Wani abu da bai samu daga iyayen sa ba sabida kawaici na masu sarauta ga 'ya'yan su. Gara ma Maimartaba akan Ya Gumsu wadda babu wani kusanci ko kankani tsakanin ta da dan nata, bata san me yake ciki ba, bata taba bincikar halayyar sa ba, ita dai burin ta ya kasance cikin gata ya samu duk abinda yake so, ya girma ya gaje sarauta. Cikin dan lokaci kankani Amb. Hassan ya canza da yawa daga baragurbin halayen Sageer sai abinda ba'a rasa ba. Shima Awaisu a nasa bangaren yana iya nasa kokarin wurin ganin Sageer ya canza munanan dabi'un sa zuwa na cikakken dalibin da ya san ciwon kansa. A karshe Awaisu ya fahimci wani abu, zai iya nasarar raba Sageer da komai, amma ba zai iya raba shi da 'yammata ba. Mahaukatan kudin da sarki ke turo masa don yayi hidimar karatu, da wadanda Amb. Ke basu lokaci-lokaci duk a hidimar 'yammatan sa yake karar dasu. Yana kuma da masaniyar cewa yana branching da 'yammata a hotel ba da sanin Amb. Hassan ba. Al'amarin ya kara kazanta ne lokacin da aka yiwa Amb. Hassan sauyin kasa, daga Egypt zuwa Amsterdam akan aikin jakadancin sa. Suka tattara suka bar Egypt suka koma can. Inda suka fara karatun doctorate degree dinsu a fannin da kowanne yake a babbar jami'ar Amsterdam. Awaisu na karantar (Social Work) yayinda Sageer ke karantar (Pure and Applied Chemistry). A duka wadannan shekarun bai kara ganin kowa nasa ba, wadanda aka haifa baya nan bai san su ba. Haka wadda aka aura a bayan sa wato Fulani Bilkisu. Bayan su akwai kwarkwarori da yawa. Sannan elder sisters dinsa biyu duk sunyi aure sun hayayyafa: Ya Maira da Mairam Murjanatu. Bayan su an haifi maza biyar, biyu Ya Gumsu, uku Ya Kirjinoma, sannan Hibbani na da Humaira da Najaatu. Bayan kammala M. Sc din su dukkan su sun samu aiki a kasar Amsterdam, Awaisu aikin asibiti yake yi yayin da Yarima Sageer ke aiki da wani mashahurin kamfanin sarrafa kayan abincin gongoni na kasar. Tuni sun manta daga gidan sarauta suka fito, sun karbi rayuwar gidan Amb. Hassan wanda bazaka taba sanin ba shi ya haife su ba. Rayuwar kasar Amstedam ta karbe su sosai, sun tara arziki nasu na kansu, ga aiki ga muhalli ga ababen hawa. Amma duk da haka a gidan Amb. Suke zaune. Tun barin sa gida sai a shekarar baya ne maimartaba da Ya Gumsu suka kai masa ziyara, bisa tsananin rokon Amb. Hassan don maimartaba yace shi har abada Sageer bazai dawo masa gida ba, ya barwa Amb. Hassan shi duniya da lahira sabida gamsuwa da irin rikon da yake musu shi da Awaisu, shi kansa Waziri bai taba bada shawarar su dawo gida ba. Sai kuma ga abinda Ya Gumsu ta zo da shi yau, na nema masa alfarmar zuwa gida yayi ko sati daya ne. Ya sake lumshe idon sa ya bude a hankali. A fili ya furta "nima ina kewar ka Muhammad Sageer, tsoron abinda zai je ya zo nake. Ina tattalin mutuncin ka a idon al'ummarka. Duk da Baban ka ya tabbatar min baka da matsala yanzu". **** A shawarar da suka yi da Waziri ya karfafe shi akan ya bar Yarima ya zo gida, koda sati dayan ne, tunda dai bazai dawwama a kasar da ba tasa ba, dole watarana zai zo gida, sannan Amb. Hassan ya tabbatar musu komai lafiya a tareda Yarima. Awaisu ne dai da yafi kowa kusanci da shi ya ce da Babansa Waziri da saura. Wazirin kuma bai gayawa sarki hakan ba don ya samu nutsuwar barin dan sa ya shiga cikin 'yan uwan sa ko yaya ne. A gefe ya saka limamin Askira da sauran malaman fada yin addu'a ta musamman akan zuwan Yarima Sageer, Allah ya kintsawa mahafin sa shi a matsayin sa na magajin sa. Da wannan sarki ya yiwa Yarima umarnin zuwa gida don yayi sati daya. A wannan lokacin Amb. Hassan ya gama tenure dinsa na aikin jakadanci yana shirin dawowa gida gabadaya, don haka tare suka soma shirin tahowa shi da 'ya'yan nasa Sageer da Awaisu, inda Amb. Hassan zai sauka a kasar shi ta haihuwa Kanon Dabo, kafun ya koma Birnin Tarayya da zama. ***** "Na ga sai wani zumudi kake zaka je gida, kamar wani special abu ne zamu je mu taras banda zafin Maiduguri, ni banda Ya Gumsu ta dage sai naje ai har abada na bar Askira kenan, tunda Alanguburo baya son gani na". Awaisu yayi murmushi yana ninke kayan Yarima yana jera masa cikin tsadaddiyar trolley din sa. Bai yi niyyar bashi amsa ba sai da ya ji Yarima ya sake yin kwafa, "ni ko satin ma bazan cika ba zan dawo, ka san nextweek akwai birthday din da na hadawa (Rose), kawai sai jin zancen tafiyar nan na yi, da na san da ita da tun satin da ya wuce mun yi mun gama, she will be 26 by next week". (Rose, yarinyar Yarima ce da yake ji da ita, 'yar asalin kasar Korea ta kudu), Awaisu ya tamke fuska kamar bai ji shi ba, ya cigaba da jera masa kaya. Daga baya kuma ya ce "ayya! Ai kawai ka tafi da ita Askira ka hada mata birthday din acan zai fi bada ma'ana" Yarima yayi miskilin murmushin sa, ya ce "me kake ci na baka na zuba? Ka zuba ido zuwa shekaru biyu zan kaita Askiran ne, amma a matsayin matata ba budurwa ta ba". Awaisu ya dauka ya fada ne kawai don ya ji dadin bakin sa, ya manta da wani hali na Yarima Sageer Yusuf Askira, duk abinda ya furta yana nufin sa ne har zuciyar sa. Amma akan zancen Rose bayahudiya bai taba kawowa Yarima da gaske aurenta yake da niyyar yi ba. A halayen Yarima in ka dauke son matan sa, sauran duka ababen sha'awa ne, Awaisu ba zai daina kiran sa (his role model) ba. Mutum ne mai muhimmanta sallah da kiyaye lokutanta, mai kirki mai kyauta, abun hannun sa bai taba rufe mai ido ba. Ga jin kan na kasa da shi, ga girmama iyaye, sannan ga kokari wajen neman na kai kamar ba dan sarki ba. Bayan kamfanin da yake yiwa aiki yana kasuwancin automobile daga Amurka zuwa Amsterdam. Duk da haka maimartaba bai taba fasa turo masa kudi duk karshen wata ba, shi Awaisun shine akan komai na kasuwancin nasa kuma kyautatawar da Yarima yake masa a ciki sai ka rantse su biyu suka mallaki jarin kasuwancin. Babban abunda ke burge Awaisu a halayen Yarima Sageer shine submissiveness, ya san shi mai laifi ne a gurin Ubangiji, amma yana yawan ce da Awaisu ya kasa dainawa, kuma yana so ya daina din, mata sun zame masa barin rayuwa da baya iya rayuwa daidai sai tare da su, don haka kullum cikin istigfari yake yana fadin yana rokon Allah yasa kada ya mutu yana aikata laifin da yake aikatawa. Ko Awaisu ya soma wa'azi, baya arguing da shi, cewa ya ke ya sani babu kyau ya taya shi addu'a. Sai Awaisu ya koma yi masa yakin karkashin kasa, don kuwa yarima tausayi yake bashi, kana sabo ka san kana yi amma ka ce ba zaka iya dainawa ba, duk yarinyar da ya gani tare da shi zai bi ta bayan idon sa ya ci mutuncin ta ya razanata akan tarayya da Sageer, wani zubin har ya ce Sageer nada cuta, ga turawa da shegen tsoro, saidai Sageer ya nemi yarinyar sa sama ko kasa ya rasa, a karshe saidai ya nemo wata, shi kuma Awaisu baya gajiya da lalatawa, kamar yadda shima baya gajiya da sake nemowa. Wannan itace rayuwar Yarima Sageer da dan uwan sa Awaisu a kasar Amsterdam. Tamkar ciki daya suka fito, sha'awar su akan komai daya ce ra'ayin su daya, sannan zuciyar su tsayayya ce akan junan su, saidai hali kowa nasa daban. Jirgin su ya sauka a filin jirgin saman Maiduguri da asubahin safiyar Litinin, zaratan matasan suka soma saukowa daga matattakalar jirgin 'AZMAN' cikin shiga ta barebarin usli, wadanda fatar jikin su ta jiku da boko da kasar sanyi, kai da ganin su ka san sun fito ne daga sarauta ta ainahi ko daga irin takun su da kasaitar su. Suna sauka motar 'Askira Emirate' na jiran su. Tun a Abuja suka rabu da Amb. Hassan da Mama Laila wadanda suka hau jirgin Kano, su kuma suka hawo na Maiduguri. Dogarawa bila- adadin duk daga motocin masarautar Askira, suka bude musu kofar motar BMW wadda maimartaba kadai ke hawan ta a gidan. Daga nan basu bata lokaci ba suka kama hanyar Askira da motar civilian mai dauke da wasu fadawan cike fal a cikin ta. Yau tun safe masarautar Askira ta tashi da bushe-bushen algaita da kalankuwa da goge irin na masarautar, baka jin komai sai tashin kirarin gidan sarautar Askira, maroka da makada daga kowane bangare na garin sun barko sun cika kofar fada, haka tun jiya 'ya'yan sarki maza da mata na nesa dana kusa sun hallara a gida dakunan iyayen su mata ba don komai ba sai don marabtar Yarima Sageer wanda ya kwashe shekaru goma baya cikin masarautar gabadaya. Mairam Murjanatu ce kawai bata samu halarta ba saboda ta yi nisa tana kasar Turkiya. Naja'atu da Humaira kusan sun fi kowa zaquwa da murnar ganin Yariman domin sune basu san shi ba, suna kanana sosai ya tafi, sai kuma jikokin gidan wato 'ya'yan Ya Maira su wajen takwas. Lokacin da motocin su suka iso fada, sai kade'kaden da bushe-bushen ya karu. Wani abu ne da Sa'ade bata saba ji a cikin masarautar ba in ba wani muhimmin abu ake ba, kamar nadin sarauta ko bikin aure. Duka-duka ma dai tun zuwan ta Askira bai fi sau biyu ta ji irin wannan ba, don haka ta gane akwai muhimmin abin da ke faruwa yau a masarautar. Tana so ta san me ake yi, amma ta rasa wanda zata tambaya, don Fulani ma tun safe tasa aka shirya Zarah suka wuce babban falon ganawar sarki da iyalin sa, inda sauran iyalin gidan suka hallara, ko ta kanta bata bi ba. Fanna ma dai ta lura yau dukkan su busy suke a cikin gida da girke-girken da iyalin gidan zasu ci da wanda za'a tarbi Yarima Sageer da shi. Don haka itama tun safe bata sa ta a idanun ta ba. Sa'ade duk ta zama curious ga son sanin me ake yi haka cikin gidan, a ranta tace yau dai zata yiwa Fulani laifi sau daya, dole taje ta baiwa idon ta abinci, iyakaci Fulani in ta kamata ta murde mata kunne ko ta mare ta. Da wannan tunanin ta dau mayafin ta, sadaf-sadaf ta fita daga sassansu, a falon daya raba sassan Fulani da inda sauran bayinta ke shige da fice ta ci karo da wasu duk suka zubo mata ido, bata ko kallesu ba ta daga kafa ta fice daga unguwar Fulani Bilkisu. Mayafin ta ta janyo ta rufe rabin fuskarta, idanun ta kawai ake gani. Ta rasa ina zata dosa? Dan ba sanin kan gidan tayi ba, daga bisani ta lura da inda bayi ke karakaina da manyan farantai, kanta tsaye ta doshi wajen. Wani babban falo ne ta ga bayin suna shiga da sundukan abinci da katon katon na lemukan gongoni, ta bi bayan su a hankali har zuwa kofar falon, sai ta zagaya ta bayan tangamemeiyar tagar gilashi ta falon ta leka a hankali. Ba zata iya shaida fuskokin data gani ba don tagar ta baya ce duk sun juya bayan su, ta dai hango Alanguburo akan kujerar mulkin sa, zagaye da shi kananan yara maza da mata har da matasan 'yammata kamar ta, a gefensa daura da shi bisa kujerar da bata kai tasa ado ba wani zankadeden matashi ne, duk da bata yi nasarar ganin fuskar sa gabadaya ba ta ga gefen fuskarsa, da dogon karan hancin sa, kalar bakar fatar sa kamar ta mutanen kasar Morocco, hular sa ta nitse a cikin tarin sumar kansa sannan fararen kayan dake jikin sa babu ado irin na sarauta a jikin su. Normal tsadadden yadi ne (filtex London) mai taushi a idon mai kallon sa, sauran mata da mazan dake zagaye dasu duk bata ganin fuskar su, amma ta shaida bayan uwarta Fulani da kalar tufafin dake jikin ta kasancewar ta san ta da kayan. Wata zuciyar ta ce "yi ta kanki Sa'ade, idan Fulani ta kama ki a gaban kowa sai ta yi miki dan banzan duka. Tunda dai kin gani taro ne suke yi nasu su-ya-su (family get together)". Wata kyakkyawar mata ta juyo tana magana da wata dattijuwa, sai ta gane fuskar ta, tana daga cikin wadanda suka je wa Humaira visiting har suka kira ta (Ya Maira). Salin-alin ta soma ja da baya, sawun ta a likkafa, sannan ta juya da sassarfa akan kafafun ta ta koma inda ta fito. Ko ba komai ta ba idon ta hakkin sa. Da Fanna ta fara cin karo ta saka bayin dake sassan a gaba tana ta yi musu fada don me suka barta ta fita, sai gata ta shigo kamar an koro ta, da sauri Fanna ta doshe ta tana hamdala. "Daga ina kike Sa'adatu?" "Kai Fanna, sai kace wata karamar yarinya zan bata a cikin gidannan ne da wayo na da idanuna da komai?" "Ba cewa na yi zaki bata ba ranki ya dade, inda Fulani ta shigo ta nemeki bata gan ki ba me kike so mu ce mata?" Sa'ade ta murguda baki tayi shigewar ta ciki tana kunkuni. "Haka kawai ayi ta kulle mutum a daki sai ka ce wani daddawa, su suna can suna jin dadin su cikin jama'a, bata so a ganni don me ta haifo ni?" Wunin ranar zungur bata ga Fulani ba, sai washegari da safe ta fito don ta gaisheta kamar yadda ta saba duk safiya in dai tana garin, ta same ta ta hargitsa bayi suna ta gyare-gyare a sassan wai Yarima zai shigo ganin Zarah, yau zai shiga kowanne sassa na gidan. Sama-sama Fulani ta amsa gaisuwar ta sannan ta cigaba da bada umarni, ta juya cikin jin haushi, ta tsani wannan rashin bata muhimmancin da Fulani take yi amma ba yadda zata yi. Bakon da ake ta shirye-shiryen domin sa bai shigo sassan nasu ba sai bayan sallar la'asar. Tana jin wani irin kirari yana tashi daga bakin bayi (Gyara kimtsi da kyau... Lafiya dan zakin duniya. Lafiya dan malafar duniya. Lafiya dan mai fada da cikawa. Lafiya dan masha-sha. Lafiyar ka dama da hauni mai nasara. Zauna dai-dai dan bawan Allah. Zauna dai-dai dan waliyin Allah. Aminchinka rike linzamin ka dan bawan Allah....zauna dai-dai dan masu Alheri...) daga bisani ta ji muryoyin mutane da alama ba shi kadai bane, mazane sun kai su biyar, bayan Yarima Sageer akwai Awaisun sa, kannen sa maza su hudu tareda Ashgar duk da ba lafiya ce da shi ba hannun sa na cikin na Yarima kamar zai maida shi cikin sa. Tana so ta yi leke tana tsoron Fulani, sai ta zo bakin kofar dakin ta ta kasa kunne ita a dole sai taji me ake yi kuma su wanene? Lol. "Yarima in a hanya na ganka ai bazan taba gane ka ba, sabida a hoto kawai nake ganin ku wajen Askirama, gara kai kana nan a bakin ka, amma Awaisu ya koma bature sak!" Inji Fulani. Awaisu yayi murmushi ya ce "duk da haka gara ni ban manta Kanuri ba, amma wannan ko Hausa da kyar yake yin ta, su sanya alkyabba kuwa tuni ya manta yadda ake yin su balle yadda zai wara kafafu ya hau doki". Yarima ya harareshi a lokaci guda yana jijjiga Zarah dake hannun sa, wadda tun ganin sa da ita jiya Allah ya sanya matsananciyar kaunar ta a zuciyar sa musamman da ya ji cewa sikila ce, yayi kissing kumatun ta yace. "Ranki ya dade da fatan zaki bani Zarah in tafi da ita Amsterdam in kin yaye ta in sa ta a makaranta?" Fulani ta ce "in ka yi aure ba? Kuma matar 'yar gida ka aura wadda bazata ji kyashin rike maka diyar ba" Awaisu ya fashe da dariya da ya tuna wadda Yarima yake shirin aure, dan kuikuiwo ne pet din ta dake biye da ita duk inda zata, ya ga yadda zata rike dan mutum sukutum ko sallah bata yi. Ta kasan ido Yarima ke kallon sa, shi kadai ya gane me yake nufi da kallon da yayi masan, don haka ya ja bakin sa yayi shiru yana cigaba da dariya. Yarima ya dago manyan idanun sa farare kal, ya sauke su a kan maridin dan uwan sa wato Ashgar, ya ce. "Ashgar, ina labari?" Murmushi Ashgar din yayi, sannan ya maimaita abinda Yarima ya ce, ba tare da ya san me ya fada ba, Awaisu yace "ya kamata ace Ashgar yana karbar rehabilitation therapy, da an samu cigaba sosai a rayuwar sa, a can kasashen da muka fito ana bawa irin wadannan lalurorin muhimmanci sosai su yi rayuwa mai ma'ana kamar kowa". Suhail dan Ya Kirjinoma yayi tsaki ya ce "da dai Ya Kirjinoma zata yarda cewa ciwo ne daga Allah mai zaman kansa, amma ita kullum zancen ta bakaken aljanu ne aka tura masa" haka hirar ta koma a kan Ashgar, Yarima da Awaisu na fadin ba wani aljanu, in maimartaba zai amince da Ashgar zasu koma Amsterdam su kai shi rehabilitation center na masu lalurar sa. Yarima ya ki ajiye Zarah a tsayin zaman su a falon, tana rungume a hannun sa, baya gajiya da kallon ta yana mata wasa jefi-jefi. Aka gabatar musu da kabakin da Fulani ta shiryawa Yarima na barka da zuwa, sosai suka ci abincin suna hira a tsakanin su cike da kaunar juna, duk cikin matan maimartaba sai yaji Fulani Bilkisu tafi kowacce samun matsayi a zuciyar sa akan dalilin da bai sani ba. Koda yake a fili yake; Fulani na da matukar kirki sannan tana kaunar 'ya'yan Askirama da zuciya daya kamar yadda yake kaunar ta. Hassada ce kawai da kishi irin na mata zasu sa ka kushe Fulani Bilkisu ko wani hali na ta, domin ita din ta yi ta kowanne bangare. Basu bar sassan ba sai ana gab da kiran sallahr magriba, shima din sai da Ya Maira ta biyo bayan su don ganin uwar da suke kullawa a unguwar Fulani Bilkisu wajen awanni biyu, tana shigowa ta ce in ya gama yaje Ya Gumsu da bakin ta na jiran sa, dole suka yi haramar tafiyar yana gayawa Fulani gobe in ya dawo daga hawan kilisar da zasu yi zai dawo ya ga Zarah. Tayi murmushi tace "Zarah na murna da dawowar wannan babban Yaya nata, mai ji da ita, bakon Amsterdam!". Yayi murmushin da ya kara masa kyau da ilhama ya sunkuyar da kai sannan ya fita, ya bar kamshin turarensa INVICTUS (by Paco Rabbanne) a sassan Fulani bakidaya. Zata wuce daki ta hango Sa'ade na leke ta tsakanin kofa, murmushi tayi tace "uwar gulma". Sa'ade bata ankara ba sai ganin Fulani tayi agabanta, sosai ta razana ta ja da baya, Fulani tace "uban me kike lekawa?" Ta zumburi baki. "Ni ba abinda nake lekawa, maganar maza na ji, nikuma na san maza basa shigowa sassan nan". Fulani tace "to ina ruwan ki da ko su waye? Ko maza na soma kawowa? Wallahi ki kiyaye ni bana son gulma, ba ruwan ki da duk abinda bai shafeki ba a gidannan don kuwa ba gidan ubanki bane, kara ki Uban su yayi". Hawaye suka ciko idon Sa'ade, ba yau Fulani ta soma cin mutuncin ta ba akan kankanin abu, amma sai ta ji na yau ya fi na kullum kona mata rai, ta yi alkawarin ta daina mayarwa Fulani magana amma tsabar bacin rai bata san sanda ta ce cikin hawaye. "Tunda kin ce inada dan uwan uba ki kaini wajen sa mana!" Fulani tace "an ki a kaiki, anan zaki zauna zaman AGOLANCI. Zaman da ubanki yake guje maki, gashi ya same ki bayan ran sa. Enjoy!". Ta fice ta rufo mata kofar da karfi. **** Ya Gumsu ta dubi Yarima yana shigowa babban falon ta, bayan dawowar su daga masallaci sallahr isha. Hararar sa ta yi cike da kauna da jin haushi, ba karamin haushi ya bata ba da ya ja kannen sa suka tafi sassan Bilkisu suka shantake bata san uwar da suke yi ba, abinda bazata taba lamunta bane wata alaqa ta shiga tsakanin Yarima da Fulani Bilkisu shima a sammace mata shi yadda aka sammace uban sa. Yana zama ta soma fada Ya Maira na taya ta "ka san tsakanina da ita ne da zaka je ka rashe a unguwar ta har ta baka abinci ka ci? Meye hadin ka da ita? Gara kowa da ita, ita ce annamimiyar gidan nan bakidaya, kai bako ne baka san komai ba don haka ka tsaya a matsayin ka na bako. Ka kama 'yan uwan ka da na haifa kadai, ban yarda da wani hadin kai na munafunci ba kowa ya zauna da wanda uwar sa ta haifa". In da sabo ya saba da halin mahaifiyar sa na kishi da korafi akan abokan zamanta, don haka bai wani damu ba har tayi iya fadan da zata iya ta bari, ta koma hirar arziki. Duk abubuwan da ke faruwa a gidan sai da ta labarta masa wanda ya shafe shi da wanda bai shafe shi ba. Har labarin Bilkisu ta dauko 'ya daga inda basu sani ba tana boyewa a sassan ta saida ta bashi "sabida ada haihuwa ta ki tsaya mata. Ka ga 'yar? Don an ce suna kama sosai" "ni ban ga kowa ba" ya fada (sounding uninterested). Sannan ya mike ya ce da ita zai je ya kwanta don a gajiye yake sosai, yau sun sha yawo. A matsayin ta na mai girki ita ke da turakar maimartaba yau. Lokacin shigar ta na yi ta bar Ya Maira da yaranta ta tafi kasancewar anan zasu kwana sai gobe zasu koma Biu. Da sallama ta shiga ta samu Alanguburo yana addua ya fuskanci alkibla. Saida ya gama ya shafa sannan ya ankara da shigowar ta dakin. Ya dube ta daga inda yake zaune ya soma magana cikin yanayin data kasa fassarawa. "A tabbatar duk bayin da aka zubawa Yarima babu mata a ciki, maza kadai na yarda suyi masa hidima har ya koma". Yanayin fuskar Ya Gumsu ya nuna bacin rai tsantsa, har sai yaushe Mai Askira zai daina yiwa Sageer kallon tsohon laifin sa? Abu an yi shi tun kuruciya amma har gobe dan ta mai laifi ne dan kowa tsarkakakke. Dubi Yarima don Allah wanke hannu ka taba me zai yi da wasu matan bayi? Ya Gumsu ta juya kai cikin takaici tace "to ayi masa aure mana! Wannan irin takunkumi haka!" Sarki ya karanto tarin bacin ran da ke cikin kalamanta, kuma ta yi maganar ne da alama ta dade ta na cin ta a zucci. An kai mata Da wata uwa duniya an yasar ba wanda ya damu da halin da yake ciki, kuma a yanzu ma ana nufin ya koma babu aure ko me? Ta san duk laifin Waziri ne, don sai abinda ya ce Askirama ke amfani da shi, idan kuwa bai ce lokacin Auren Yarima yayi ba Mai Askira ba zai taba zancen auren nasa da kansa ba sabida kawaici irin nasa. "Me kike ci na baka na zuba Fulani! Akwai abinda nake jira ne, zuwa wani dan lokaci da zai dawo gida bakidaya". Nan da nan fuskar Ya Gumsu ta washe, wani farin ciki ya bayyana akan kyakkyawar fuskar ta. Ta gyara zama tace "Alanguburo sai a san daga masarautar da ya kamata a dauko masa mata tun yanzu, ni in son samu ne na fi son masaurautun wajen Borno, kamar Kano da Bauchi, su ne kawai zan ce masarautun su sun fi namu, kuma auratayyar mu da su zai karawa masaurautar Askira kima a sauran masarautu tsararrakin ta". Sarki Yausufu sauraron ta yake absent-mindedly a daidai lokacin da wani bakon tunani ya bakunce shi. Ya Gumsu sai gani ta yi ya miki zuruf! Kamar an tsikare shi ya nufi hanyar waje. Sai kawai ta biyo shi don abu ne da bai taba yi ba fitowa a lokacin da ya riga ya shiga barci. Sai gani tayi kai tsaye ya doshi sassan Yarima Sageer cikin takun shi na alfarma. Yana so ya tabbatar da idanun sa. Yarima lafiya yake zaune ko yau ma ya kama 'ya'yan mutane ya danne. Dogarawan da ke gadin bangaren Yarima tuni suka wangale kofofin suna bawa Sarki da Ya Gumsu hanya, da suka doso dakin barcin Yarima sai maimartaba ya dauke karar sawunsa, sadaf-sadaf yake takawa yayin da Ya Gumsu tashin hankalin bata san me Yarima yake ciki ba ya dugunzuma zuciyar ta. Sarki na zuwa ya danna kai dakin da ya tabbatar yana ciki, sai ya same shi bisa darduma yana sallah. Ya Gumsu na iya jin nannnauyar ajiyar zuciyar da Alanguburo ya sauke, ya yarda ko Yarima bai daina halin sa gabadaya ba akwai improvement kashi 70% cikin halayen sa na yanzu, wanda ya kara masa karfin gwiwa akan sabon tunanin da ya bakunce shi a daren yau ba tareda ya taba kimsawa zuciyar sa ba. Ya kudure kafin ya gabatar da kudirin sa ga kowa zai yi istikhara ya nemi zabin Allah. Juyawa yayi ba tare da ya ce komai ba, itama Ya Gumsu ta bi bayan sa. Da sa'an maganarta ne cewa zata yi "a dai dinga kyautatawa dan adam zato". Da ba sa'an maganarta bane sai ta kumshe abarta a cikin ta tana kunkuni cikin ranta "haka kawai kamar shi kadai ne fitinannen da a gidannan". Ta manta cewa adadin soyayyar ka akan mutum, adadin damuwar ka gareshi. Sannan 'ya'ya ababen kiwo ne ga iyayen su wannan umarnin Ubangiji ne. Mai Askira bai kwanta ba a ranar sai da ya gabatar da sallahr istikhara akan kudirin dake zuciyar sa. Ita kuma Ya Gumsu ta kwana zuciyarta kal, a kalla dai daga yau zai sassauta zargin Yarima a ransa. **** Kwana biyu kenan Sa'ade da Fulani basu hadu ba, kowacce fushi ta ke da 'yar uwarta. A jiya Yarima ya kara shigowa kamar yadda yayi alkawari amma bai dade ba Ya Gumsu ta ishe shi da aiken kira dole yayi sallama da Fulani ya tafi. Yau dai Sa'ade ta yiwa kanta fada bata yi musu labe ko leke ba, amma tana jiyo tashin sautin muryar Yarima mai kauri da zurfi (husky) a lokacin da yake magana da Fulani. Ta fahimci ko ma wanene bakon nan mai matsayi ne sosai a gidannan, tunda har yake shiga ko'ina ba shamaki. "Idan ka kara shiga unguwar ta Allah ya isa ban yafe maka ba!" Ya Gumsu ta fada a zafafe tana numfarfashi, munafukar baiwar ta ta gaya mata abinci Bilkisu ke bashi yana ci wanda basu san me aka zuba a ciki ba. A firgice ya dago ya dubi Ya Gumsu. "Me yayi zafi haka Ya Gumsu?" Ta harareshi kamar idanun ta zasu fado, ai har gara ya likewa Hibbani akan Bilkisu, itace ta dauketa mutum take kuma bata girmanta na Gumsun gari, ba wannan mai yiwa kowa kallon bai isa ba, bayan bata aje musu komai ba sai katon kashi da 'yar da ita da babu duk daya. "Ubanka ne yayi zafin, nace Ubanka ne yayi zafin Yarima!". Ba shiri ya sadda kansa, amma hakika ya firgita da kalamanta, ya kuma tabbatar kishin ta da Bilkisu ba dan kadan bane don sauran matan ma ai ya shiga unguwar su amma ko sau daya bata yi magana a kai ba. "Allah ya huci zuciyar ku Ya Gumsu, in kun yi hakuri ni da ba mazauni ba tafiya zan yi babu mai sake gani na nan kusa". Ya juya ya fita ba tare da ya bi ta kan abincin data shirya masa ba. Koda ya koma bangaren sa ransa a bace yake, baya son wannan halin na Ya Gumsu tun yana karami, balle yanzu da ya girma ya mallaki hankalin kansa. A ganin sa a matsayin ta na babba kuma Gumsun gari kamata yayi ta kama girman ta ta rungume kowa dake karkashin sarki, tunda shi ya dauko da kansa ya kawo ya hada cikin iyalin sa to tabbas yana so ne. Ya samu sako daga jakadiyar sarki cewa maimartaba yana son ganin sa gobe kafin ya shiga fada. Wanka ya shiga sannan ya fito ya sauya zuwa pajamas, Awaisu ya kira a waya yana daga tsaye jikin taga "kana ina ne?" Awaisu yace "gani nan tare da Ba'ana (mahaifiyar sa) tana min hira, amma yanzu zan taho, hirar tata dai duk guda daya ce tun isowar mu bata wuce ta aure, wai har matar ta zaba mini" murmushi Sageer yayi, ya ce "ai gara a taimakeka a lullube a kaiwa wata mai tsautsayin, in ba hakan ba a haka zaka tsufa baka taba morar kuruciyar ka ba". Awaisu ya ce "gara in tsufa a hakan dai, Allah ya gani ban taba 'yar kowa ba balle in na haifa a taba min tawa". Sageer ya san magana ya gaya masa don haka ya cillar da wayar bayan ya ce da Awaisu "don't show me your ugly face, sai na neme ka".. Washegari bayan ya shirya cikin sababbin dinkunan da maimartaba ya aiko masa dasu, sai kamshin invictus ke tashi a dakin, ya fuskanci alqiblah ya sallaci sallahr Dhuha. Idan akwai wata dabi'a mafi kyau cikin dabi'un Yarima Sageer to sallahr farillah ce akan lokaci da kokarin yin nafilfili babu gajiyawa. Ba ya yin sallahr farillah kadai ba tareda ya hada ta da nafila ba. Sannan sallahr "Dhuha" bata wuce shi komin busyn da yake ciki. Karfe tara daidai ya tasamma turakar mahaifin sa, inda duk ya gifta sai ya bar kamshin turaren sa Invictus (Paco Rabbanne). Inda duk bayi suka ci karo da shi sai sun fadi sun yi gaisuwa sun yi masa kirarin da suka saba yi masa, a haka cikin takunsa na kasaita da sassarfa har ya isa falon da sarki ke ganawar sirri da iyalin shi. Tare da Ya Gumsu ya same shi yana karya kumallo, ta sha ado cikin koriyar laffayan matan Kanuri, bai taba ganin Ya Gumsu da wata suttura da ba laffaya ba, da alama yau maimartaba cikin nishadi yake, nishadin nasa baya rasa nasaba da kyakkyawan sauyin da ya gani a tare da Sageer tun zuwan sa, da kuma na kyakkyawan kudirin dake zuciyar sa. Yarima Sageer ya zube yana kwasar gaisuwa wajen iyayen sa, su kuma suna amsawa with so much affection wanda ya bayyana karara akan fuskokin su, maimartaba ya zuba masa ido cikin murmushi ya ce. "Kamar ba Sageeru na ba, Sageer wanda ya tafi ya barni dan firit da shi kamar a bushe, wannan dake gabana ai babban mutum ne wanda ya kamata ace zuwa yanzu ya ajiye mata hudu da kwarkwarori a gefen sa". Murmushi mai kayatarwa Yarima yayi, wanda ba kasafai ya ke yin sa ba, ya sake sunkuyar da kansa. Sarki Yusufu ya dan tsura masa ido kafin ya kira sunan sa cikin sigar son ya bashi hankalin sa. "Muhammad Sageer. Kafin mu yi kowacce magana ta aure ce kan gaba, yanzu babu abinda nasa a gaba banda burin auren ka. Duk wani kyakkyawan kudurin mu akan ka ya cika. Ina fatan zuwa yanzu ka samu nutsuwar da kake ganin zaka iya zama da iyali?" Yarima ya muskuta cikin jin nauyi, kansa a kasa bai ce komi ba, aure baya gaban sa ko kadan, don a ganin sa yanzu ne yake cikin twentieth din sa, ya ke cin kuruciyar sa da duk irin macen da yake so, aure zai zamo tamkar takura ne da takunkumi a gare shi, amma what if Maimartaba zai yarda ya auri zabin ran sa, Rose? In ita ya aura bazata takura masa ba, zata bar shi ne yayi rayuwar sa yadda yake so. Ya ga cewa wannan itace damar sa ta karshe da zai samu ya gabatar da zancen ta. Idan wannan damar ta wuce mawuyaci ne ta sake zuwa. Don haka ya tattaro dukkan courage din sa, ya ce. Ya gyara zama ya fuskanci Baban sa. "Alanguburo (Allah ya kara maka yawan rai) akwai yarinyar da na yi wa alkawarin aure a can Amsterdam, kusan shekara guda muna tare". Sarki Yusufu ya ji gwiwar sa ta yi sanyi, kuzarin jikin shi ya kare. Me yasa ya fara tambayar sa kafin ya fada masa na sa kyakkyawan kudurin akan sa? Yanzu duk abinda zai ce bayan wannan da Yarima ya fada zai zamo tamkar yayi imposing dinsa ne ga auren da baya so, tunda ya ce yana da zabin sa tuntuni, zai zama auren force....wanda baya cikin tsarin sa, bai taba yi wa 'ya'yan sa auren dole ba daga matan har mazan. Kenan dole a matsayin sa na Uba mai muhimmanta hakkin farin cikin 'ya'yan sa da ya rataya a wuyansa kuma shugaba mai adalci ya bawa Yarima dama ya auri zabin ransa. Kamar yadda nasa iyayen suka yi masa. "Kana da damar auren zabin ranka Yarima, Allah yayi albarka". Ya Gumsu ta tattare gira tace "haba Mai Askira? Haba Askirama? Haba gatan Askira? Yaya ba'a binciki gidan da ya nemo auren ba za'a amince masa da gaggawa haka???" "Ko a ina ya nemo in dai yana son ta shike nan" Yarima ji yayi kamar ya rungume Baban sa, saidai duk da haka yana cike da fargaba, shin mai Askira zai amince ya bashi goyon baya idan ya ji cewa Rose bayahudiya ce wadda bata da addini koda na kiristanci ne? Ya Gumsu ta kasa hakuri, ta ce a kagare "sai ka fada mana su waye iyayen ta, 'yan wace masaruta ne? Sannan daga wace kabila ta fito?" Jin Alanguburo bai ce komai ba ya fahimci shima yana son jin amsar. Mu karasa a littafi na biyu. Tare suke. Taku har abada: Takori