﻿[5/22, 9:58 PM] Miss Xoxo: *_MASARAUTA_*
 _(A cindrella story) _
           👑 💘

_*NA_*


_*NANA HAFSATU_*

_wattpad:missxoxo00_
_Arewabooks:mssxoxo_

_*ZAFAFA BIYAR 2002_*
_PAID NOVELS/LITTATTAFAN KUDI NE_


_*FREE PAGE: 1_*

_بِسْمِ اللهِ الرَّحْمنِ الرَّحِيمِِ _

_Wannan littafi kirkirarre ne, Sunaye, garuruwan ciki da sauran abubuwan daya kunsa idan sunyi shige da rayuwar wani ko wata to akasi aka samu. A gafarce ni. Sannan bloggers , YouTubers da sauran su, Dan Allah kada a daukar min littafi ayi amfani dashi ba tare da izini na ba. Duk wanda yayi hakan nabar shi da Allah. _

••••. <><>••••• 

*YANKIN KINDAU*

*TSANGAYAR GWANI TSAYYABU*

   ×××Zaune gwani tsayyabu yake, Ya harde kafafuwansa. Sanye cikin babbar riga ba yar cikinta. Sai wandon rigar kalar sararin samaniya.

Hular kansa irin tashi ka fiya nacin nan ce. Hannunsa rike da sharbaceciyar bulala yana dagata sama da kasa .

Almajiran dake gabansa kowanne ya langabar da kai cike da fargabar kar dorinar sa ta ruguza akan su. Sai kururuwa murya suka sake yi dede lokacin da gwani tsayyabu ya mike yana maimaita.

"To kai, To kai..."

"minjaye , Nu'ara, Alu, hasabe, shimmeruwa, Ya, Mi, Ara. Aya. Alu, an, baki, waw, zal, baki, lallan, hakuri. .."

Suna fada yana kada kai. Dai dai lokacin da ya hango Gwani Dauda yana tahowa wajen sa. Sai zabga sauri yake yi 

"A tsaya, Ina Rabilu?"

"Iya gida innani ta aiko an kiran sa. " Cewar Musaddiqu qani ga Rabilu. 

"To kai masa jiranye kafin ya dawo. Ayi karatu dakyau. Idan 10 tacika atashi atafi gidajen aiki. Karfe 2 adawo anaji ko?"

"Eh!"

Da sauri ya fuce daga yar langalangar kwanon da yake koyar da almajiran nasa aciki. Dogon kwano ne da bai cika fadi ba . Don haka aka rabashi biyu. Rabin sa suke karatun aciki. Daya rabin kuma wajen kwanan su ne. 

 "Barka da safiya Dauda " ya karasa fada yana mai mikawa gwani Dauda hannu sukayi musabaha.

"Barka de . Baka shirya ba kenan. "

"Afuwan. Yar cikin kawai zan zuro yanzu agida mu wuce. Se mu hau achaba don muyi saurin samun daurin auren ko.?"

"Ai se 11:30 idan muka yanke ta cikin bingi nan da nan zamu isa.Ba sai mun batar kudi ba Insha Allahu "

"Hakanma yayi. Bari na zuro rigar. " Gwanni tsayabu na karasa magana ya haye dan dakalin dake kofar gidan sa ya shige. 


**GIDAN KWANO**


Harira da Naja matansa kowacce na zaune daya na kallon gabas daya yamma. 

Tunda suka amsa sallamarsa kowaccensu ta juyar da kanta gefe tacigaba da abunda take.

Daga labulen dakin harira yai ta mike da sauri tana janye hannun nasa.

"Malam ya haka kuma? Ko kayi ajiya ne bansani ba? Sarai de kasan ba kwana na bane bare kace kayi mantuwa."

"Karma ka soma budemun daki. Babu komai naka aciki " cewar Naja dake susar kunne da gashin kaza. 

"Ah malam ka shigo? Sannu da dawowa. Kayi hakuri ina cikin bayi ne." Cewar amaryar sa zaituna Wadda tafito daga cikin bandaki. Tayi daurin zani. Sosonta na rataye a kafadarta. Hannunta daya Kuma yana rike da kwandon wanka da sabulu.

Naja dake can gefe taja dogon tsaki tana yatsina. Harira kuwa fuuu tashiga cikin kuryar dakinta tana mita.

"Shigowa ta kenan yar albarka. "

"To malam sannu da dawowa. Mu shiga ciki ko?" Ta karasa fada tana mai dage yamfadin dakinta. 

Ya dan saci kallon Naja ta wutsiyar idanu ganin yadda tacika tayi fam tamkar zata fashe hakan yasa gwani tsayyabu hanzarin girgiza kai domin baya son tashin hankali.

"Yi sauri ki miko mun rigata yar ciki, Nan na barta ko?”

Zaituna ta shiga duddubawa, Can saman gadonta ta hango rigar a ninke. Ta dakko hade da turarenta na ruwa ta shafe rigar da shi.

Ta zura hijabi ta fito da rigar a hannunta,

“Gashi Malam….”

“Yauwa yar albarka. Sai kamshi take. Nagode miki.”

Nan da nan ya zura rigar, Hade da janyo nera dari biyu cikin aljihun sa.

“Gashi wannan a sayo kayan miya, Ai shine kadai babu ko?”

“Eh komai akwai Malam, Shinkafar ma Za’a dafa yau a dafa gobe da yardar Allah bata kare ba. “

“Toh Masha Allahu. Naja’atu yaran nan basu dawo bane.”

“Kawai dai kace yar gabon goshin naka bata dawo bane?”

Girgiza kai kawai yayi, Ya dan saki murmushi, Can kasan makoshi ya furta,

“Allah ya kyauta. Ni na tafi, Semun dawo.”

“Toh Malam Allah ya kai ku lapia ya dawo daku lapia. Mu ma idan rana tayi sanyi zamu leka wunin.”

“Aamin, Hakan nada kyau.”

Har kofar fita waje zaituna taiwa gwani tsayyabu rakiya. Sannan ta koma cikin gidah. 


**INTEESAR*


**

 Ina tafe ina tankadi da bokitin da yake kai na ina ‘digirgire da shi. 

Wanki mukayi a kogin bagaja. Nagaji liqis, Allah Allah nake mu karasa gidah saboda gajiar da muka kwaso. 

“Intee, Ni kuwa ya kukayi da Malam isubu? “

“Waye Malam isubu.?” Na kalli indo yayata ko nace kusan sa’ata. Ina gatsina fuska.

“Kutuma. Malamin naku yau kuma shine baki sani ba.”

“Au ho, Mugu zakice mun. Canta matse masa. Ni na manta da babun sa sai yanzu da kika budo shi.”

“Ai Intee yar renin hankali ce.” Fatsima kanwata tafada tana tafa hannuwa. 

Daria muka kece na taune kasan lebe na, Hadi da gyara zaman zanin da ke daure ajiki na. 

Muka cigaba da tafiya muna hira, Munzo dabdalar samarin yankin mu, Sai ga Adamcy wai shi bai yarda ba masoyi na. Se buda kafada yake yana takowa wajen mu. Na dube shi tamkar na feffella masa mari saboda bakin ciki. 

Ya ajiye boko yace ba zeyi ba, Shi ba arabin ba, Bayan maza kadai ake bawa yancin yin boko a yankin mu. Ina matukar son karatun boko amman ba damar nayi. Inaji Ina gani dole na hakura. Duk kuwa da babu ranar da zatazo ban roki Allah bukata ta na sonyin karatun boko ba. 

“Masoyi yahhhhhh…”Cewar adamcy yana wani kanne idanu. 

Naja dogon tsakin dana tattaro tsawonsa tundaga ruwan cikina zuwa baki na. Hade da dankara masa harara.

“Au kwafsii.. Yayar mu ina kwana, Kanwata an wuni lapia.?” Ya rissina yana gaysar da Indo, Dake murmushi. 

Suka amsa shi. Ni kuwa saboda takaici gaba nayi tamkar zan tashi saboda sauri. Sai jin iskar wucewar sa nayi ta kunne na. Ya karbi bokitin hannu na yana murmushi,

“Haba tagaban goshin Adamcy, Ki dena wahal mun da kan ki. Nafa gaya miki duk sanda zaki wanki, Na zama mawankin ki, Zan wanke miki kayan ki, Na durje su na sabe miki, Kana na kaiwa Buhari me guga ya goge miki su sab..”

Ai ban bari ya karasa ba nayi gaba abuna ina jan tsaki. Da naga yana kokarin cinmani a sauri, Na Kara kwasa aguje na shige gidan su Wasila kawata. 

Haka yaita buga nacinsa a kofar gidan na hana wasila da kannenta zuwa wajen sa. Don kansa ya gaji ya aiko yaro da botikin nawa da kuma awarar dijama ta wazobia……

×ZAFAFA BIYAR×

pAGES 1K 1page kullum books biyar.

Pages 2: 3k vip group .

Vvip ta pc:3500.


Talla saman page:1k

Tsakiya 800

Karshe 500.


ZAFAFA BIYAR*


*_KUFAN WUTA_*
_Safiyya Huguma_

*_BAQAR INUWA_*
_Billyn Abdul_

*_RAYUWAR MACE_*
_Hafsat Rano_

*_MASARAUTA_*
_Miss Xoxo_

*_NOOR ALBI_*
_Mamuhgee_

Bilkisu Ibrahim Musa
1487616276
Access bank

Number shaidar biya👇🏼

*_09032345899_*

*KATIN MTN*

09166221261


MSS XO WRITES❣️
[5/22, 9:58 PM] Miss Xoxo: _*MASARAUTA*_
_(A Cinderella story)_
           👑💘

   _FREE PAGE: 2_

_NA:_


®️ _NANA HAFSATU_

©️ _ZAFAFA BIYAR WRITERS_


_wattpad:missxoxo00_
_Arewabooks:mssxoxo_

_BUSINESS:👇🏾_

_YERWA INCENSE AND MORE: MASARAUTAR KAMSHI:_

_THE SCENTS WITH DIFFERENT ESSENCE FOR YOU AND YOUR HOME_

_DO YOU WANT THAT MAIDUGURI AND SUDANIAN SCENTS THAT LASTS LONGER AND LINGERS? YERWA INCENSE AND MORE GOT YOU AND YOUR BELOVED ONES COVERED WITH LUXURIOUS SCENTS. KAMSHIN YAN YERWA DA SUDAN💘🙏 20% OFF ORDERS. MUN CIRE KASO 20 NA KUDIN KAYAYYAKIN MU_

_KHUMRAHS_
_KULACCAMS_
_TURARUKAN WUTA_
_NA TSUGUNNO_
_NA KAYA_
_NA GIDAH_
_NA GASHI_

_NA WANKA_
_NA WANKI_
_NA MOPPING_

_AIR FRESHENER_
_CURTAIN AND CHAIRS SPRAY_
_WARDROBE BALLS_
_SCENTED PEBBLES_

_ARABIAN OIL PERFUMES_
_HAIR SPRAY AND CREAM_
_DILKE AND HALWA SET_

_KABBASA_
_BURNERS_
_KASKO_
_TONGS_
_COAL IGNITERS_

_SKIN CARE PRODUCTs_
_OUR TURARE SAMPLE SETS_
_BRIDAL SET (SAITIN AMARE)_
_KUJERAR TSUGUNNO_

_SABULAI NA GYARAN JIKI DA SAURAN KAYAYYAKIN GIDAH NA KAMSHI . KOMAI DA KOMAI AKAN FARASHIN SARI KO SAYI DAYA DAYA_

_MUNA TURA KAYAYYAKIN MU A KO’iINA A FADIN NIJERIYA DA KETARE_

_SIYAN NAGARI MAI DA KUDI GIDAH, 100% TESTED AND TRUSTED_

_instagram:yerwaincense_and_more_*

_WhatsApp: 08095215215_

__

×××Ina baje akan tabarmar gidan su Wasila mun gama cinye awarar da Adamcy ya aiko da ita. Na mike ina gantsare bayana. Saboda yadda hakarkari na ke ciwo tsabar durkushen wanki.

Yarkaccacciyar akuyar gidan su Wasila tayo kai na tamkar zata ciza. Nasa kafata na shureta ina had'e fuska.

"Idan talaka ne kai. Kowa da komai raina ka yake."

Innar su Wasila dake gefe tana tankade tayi daria.

"Ke Kuma da wa yar albarka?"

"Da akuyar nan mana Inna. Kamar mayya zata cinye mun kafa. Banda tsabar reni ta isa tayiwa masu kudi haka?" Na juya na gallawa akuyar harara hade da gatsine baki. 

Inna tayi dariya kawai tana girgiza kai,

"Sabo ne kawai da tayi da ku. Kudi kuma da yardar Allah yar albarka wataran sai kin bawa wasu ma kyauta."

Sosai naji dadin adduar da innar su Wasila ta mun. Na dashare baki na saki murmushi kawai ina mai jujjuya zobena dake karamin yatsana na karshe. 

Na zundumawa Wasila kira dake can kuryar daki tana neman hijabin da zata mun rakiya .

"Ke ni zan tafi. Bar rakiyar."

"Haba kawata"

"A'ah ba za'ai haka ba, Ke Wasila zo ga nawa jikin taga ki dauka ki mata rakiya har gidah." Cewar innar su. 

Da sauri Wasila ta fito ta zura hijabin muka tafi , Bayan nawa innar su sallama.

Muna tafe a hanya muna hira. Ba wani tazara bace sosai tsakanin gidan su da gidan mu . Amma dake hirar bamason ta Kare ba kuma ma so mu rabu, Sai muke tafiyar ahankali. Bokitin kayan wanki na na dauke a hannun Wasila. 

Har kofar gidah tamun rakiya. Muka tsaya a kofar gidan namu muna masu cigaba da hirar mu. Wanda rabin hirar dik zancen wulakancin da Fati kawar mu tayi mana ne. Babar su ta haihu, Fatin tahada pati ta gayyaci kawayen mu yan gayun yankin mu mu kuwa bata gaya mana ba , Su kaci biskit da su lemon kwalba ance har da cincin da kankarar lemon leda ta bakin kasuwa. 

Naja kwafa hade da daga hannu sama na nanawa cinyata duka bayan na kwararo rantsuwa na dire.

"Ai Fati zataci kwal haka kaza na ubanta. Gidan ta tabo. Ko a islamiyya ta nuna ta sanni sena mata dukan kawo wuka, Shegiya da kai runtume-me uwa randa "

Wasila ta kece da dariya. Ta bani hannu muka sake tafawa. 

Daga can lungu na hango baban mu yana tahowa da yar leda a hannun sa. Ai ban bari mun karasa hirar mu da Wasila kawata ba na tafi wajen sa aguje Ina murna.

"Baban mu sannu da zuwa"

"Yauwa yar albarka . Ba dai sai yanzu kuka dawo ba?"

Na sosa kai ina girgiza shi a tare. 

"Na tsaya gidansu Wasila munyi wasa"

"Masha Allah. To Allah yayi albarka. "

Wasila ta karaso wajen mu ta durkusa ta gayar da baban mu. Ya amsa mata fuskar sa dauke da fara'a.

Nan yabar mu tsaye zai shige cikin gidah na figi bokitina dake hannun Wasila nayi cikin gidah da gudu ganin yar bakar ledar dake hannun baban mu. 

Wasila dake tsaye ta girgiza Kai kawai tana daria kafin ta juya ta koma gidan su. 

  ×××GIDAN KWANO×××

  Ina shiga gidah na rafka sallama. Hade da zubewa akan kujerar Inna Harira. Da sauri tayo kai na tana makamun harara.

"Daga min kujerar uwar sarkin yan hankali. Daga tashi na kin dora wadannan kazaman duwaiwan naki akai. Bayan kashedin da nake rafka miki akan karki sake zama akan kujera ta. Tashi ina magana kin zubamun wannan idanuwan naki na mujiya." 

Tunda ta fara magana na zuba idanu kawai ina kallonta, Duk rashin tsafta ta nafi Inna Harira . Domin haka kawai seta jera kwanaki bata wanka bare wanki.

"Kaii, Tashi dan kunzugurin buroaban ki. Ina magana kin zubamun idanu. "

Zumburo baki nayi gaba, Ta yo kai na zata dakeni nayi wajen Babanmu da sauri. Ya sha gabanta yana bata hakuri 

"Aikin kawai. Yo ai dama kai ka bada dama ta rena mu. Tsintacciyar mage dai ba ta mage. Ka dinga fifita yarinyar da ba yar cikin ka ba akan 'yayan ka. "

Maganar Inna Harira ta doke ni kwarai matuka. Nayi hanyar dakin Umma ina mai danne hawayen da ke san kufce mun. 

Umma zaituna dake shiryawa a daki tayi saurin riko ni ta rungumo ni jikinta. Kukan dana keson boyewa ya kufcemun. Duk kuwa da karancin shekaru na, Rashin sanin tushe na sam bayamun dadi. Gorin da akemun nagaji da shi  Murya ta na rawa nace,

"Umma, Dan Allah waye mahaifi na ne? Menene tushe na, Taya akai aka same ni Umma? Wacece ni? Umma ki gayamun tushe na, Ko ni din she..."

"Kar ki karasa fada Inteesar, Kar na sake ji. Kema 'ya ce kamar kowa, Haifar ki akayi kamar yadda aka haifi kowa, Kina da tushe da usuli me kyau da yardar Allah. Bar kuka kinji diyar kwarai. Allah ya miki albarka." 

Kuka na na share, Na shiga kada kai na alamar toh. 

"Ga abincin ki can cikin kwanon ki. Maza wanko hannun ki kici kinji."

"Zo nan uwata." Babanmu ya kirawo sunana. Na share hawaye na na fita tsakar gidah wajen sa.

Takardar kifi ya mikomin daya kakkasawa kowa.

"Rike ke dana umman ku."

"To mungode Allah ya saka da alkhairi."

"Aamin"

Daki na koma bayan na wanke hannuna. Umma ta raba mana namu kifin. Na shiga yaga da fatar ina hadawa da abincin inaci. Kwan kifin kuma na dagargajewa mageta shi a takarda da abincin na ajiye mata taci idan tadawo daga yawon ta. Ina kaunar yar mageta, Jinta nake tamkar kanwa ta ta jini. 

××× Ina daga kwance a daki na fara jiyo muryar Babanmu yana bawa su Inna labari kan makarantar maza da zaa gyara ta boko wadda zata zama za'a dauki har yara mata. Masarautar birni ce ta dauki nauyin komai. Ina karasa ji na fita da gudu ina haki.

"Babanmu me kace? Makaranta? Boko? Mata? Kowa kenan ze iyayi?"

Babanmu yayi murmushi hade da kada kansa. 

"Shakka babu uwata. A dan guntun ilimin de da nake da shi. Makarantar ma sunanta yana nuna taci sunan marigayi sarkin birni na baya. Mai taken: SARKI ALIYU (ALKALI) MEMORIAL JUNIOR/SENIOR SECONDARY SCH. KINDAU)"

Ai ban bari ya karasa magana ba. Na figa nayi waje aguje, Ban tsaya ko ina ba se gangaren makarantar maza ta boko. Inda naga anata fashe fashe ana sauke kayayyakin gini. Bansan sanda na barke da hawayen da nake da tabbacin na farin cikin bane. Banda hamdala ba abunda nake maimaita wa cikin zuciya tah...


**ENGLAND**
LEICESTER CITY TOWN OF LEICESTERSHIRE (EAST MIDLANDS)


_
MASARAUTA (LABARIN SOYAYYAH) YANA AREWA BOOKS👇

https://arewabooks.com/book?id=6284e72eef85a63a21dbc5f5

SO DA ZUCIYA

SHIMA YANA AREWA BOOKS👇

https://arewabooks.com/book?id=623f824f9c4af77be0e96e3d

🥰😍
_ZAFAFA BIYAR!! ZAFAFA BIYAR!! ZAFAFA BIYAR!!_

_ASSALAMU ALAIKUN MASOYA MAKARANTA LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_

_BARKAN MU DA SALLAH, ALLAH YA MAIMAITA MANA, AAMIN_

_KU MATSO KUSA, ZAFAFAN NAKU SUN SAKE ZABUROWA DA ZAFIN SU KAMAR YADDA KUKE KAUNAR SU._

_WANNAN KARON MA SUNZO DA WANI SALO MAI NUTSUWA HADI DA ZAFAFAN DARUSSA NA RAYUWA KANA DA FADAKARWA AKAN RAYUWAR YAU.. BANGAREN KOGIN KAUNA KUWA BAA MAGANA. DOMIN WANNAN KARON SUN SAKE TAHOWA DA ZAFAFAN KAUNANNAKI MASU NARKE ZUCIYOYI._ WANDA ZASU ZO MUKU  IN SHA ALLAH 

_KADA KU MANTA ZAFAFAN NAKU DE SUNE KAMAR HAKA_

_SAFIYYAH HUGUMA: TAZO DA NATA SALON MAI SUNA: *KUFAR WUTA*_🥰

_BILLYN ABDULL TA ZABURO DA WANI TAKEN MAI SUNA: *BAQAR INUWA.*_😍

_MAMUH GEE ITAMA WANNAN KARON TA SAKE TAHOWA DA: *NOORUL-ALB*_🥰

_HAFSAT RANO WANNAN KARON TAZO DA NATA RUBUTUN MAI SUNA: *RAYUWAR MACE*_❣️

_NANA HAFSATU (MSS XOXO) WANNAN SALON MA TAZO DA : *MASARAUTA*_😍

***_DUKA LITTAFAI BIYAR ZASU ZO MUKU NE AKAN FARASHIN YADDA SUKE KAMAR KODA YAUSHE_*

_BIYAR : DUBU DAYA (1k)_
_HUDU: 700_
_UKU: 500_
_BIYU: 400_
_DAYA: 300_

_AKWAI TSARIN VVIP SUITES GA MASU SON HAKAN. FARASHIN SU DABAN, DOMIN KARIN BAYANI SE A TUNTUBE  MU TA: _

*_ZAKU BIYA KUDINKU ANAN👇👇_*

Bilkisu Ibrahim Musa
1487616276
Access bank

Number shaidar biya👇🏼

*_09032345899_*

*KATIN MTN*👇👇 

09166221261

YAN NIJAR 👇

+227 95 16 61 77

Ga 'yan nijer zasu tura katin moov ko Airtel zuwa wannan number
______________________

ZAFAFA BIYAR

VVIP SUITES : 3500 (PC/TA PRIVATE KAI DAYA)

VIP SUITES : 3K (VIA GROUP) A VIP GROUP ZAA DINGA TURAWA.

TWO PAGES DAILY
INSHA ALLAH!! MORNING/NIGHT. SAFE DA DARE.


*_TEAM ZAFAFABIYAR_*

_MSS XOXO WRITES ❣️_
[5/22, 9:58 PM] Miss Xoxo: _*MASARAUTA*_
_(A Cinderella story)_
           👑💘

   _FREE PAGE: 4_

_NA:_


®️ _NANA HAFSATU_

©️ _ZAFAFA BIYAR WRITERS_


_wattpad:missxoxo00_
_Arewabooks:mssxoxo_

_BUSINESS:👇🏾_

_YERWA INCENSE AND MORE: MASARAUTAR KAMSHI:_

_THE SCENTS WITH DIFFERENT ESSENCE FOR YOU AND YOUR HOME_

_DO YOU WANT THAT MAIDUGURI AND SUDANIAN SCENTS THAT LASTS LONGER AND LINGERS? YERWA INCENSE AND MORE GOT YOU AND YOUR BELOVED ONES COVERED WITH LUXURIOUS SCENTS. KAMSHIN YAN YERWA DA SUDAN💘🙏 20% OFF ORDERS. MUN CIRE KASO 20 NA KUDIN KAYAYYAKIN MU_

_KHUMRAHS_
_KULACCAMS_
_TURARUKAN WUTA_
_NA TSUGUNNO_
_NA KAYA_
_NA GIDAH_
_NA GASHI_

_NA WANKA_
_NA WANKI_
_NA MOPPING_

_AIR FRESHENER_
_CURTAIN AND CHAIRS SPRAY_
_WARDROBE BALLS_
_SCENTED PEBBLES_

_ARABIAN OIL PERFUMES_
_HAIR SPRAY AND CREAM_
_DILKE AND HALWA SET_

_KABBASA_
_BURNERS_
_KASKO_
_TONGS_
_COAL IGNITERS_

_SKIN CARE PRODUCTs_
_OUR TURARE SAMPLE SETS_
_BRIDAL SET (SAITIN AMARE)_
_KUJERAR TSUGUNNO_

_SABULAI NA GYARAN JIKI DA SAURAN KAYAYYAKIN GIDAH NA KAMSHI . KOMAI DA KOMAI AKAN FARASHIN SARI KO SAYI DAYA DAYA_

_MUNA TURA KAYAYYAKIN MU A KO’iINA A FADIN NIJERIYA DA KETARE_

_SIYAN NAGARI MAI DA KUDI GIDAH, 100% TESTED AND TRUSTED_

_instagram:yerwaincense_and_more_*

_WhatsApp: 08095215215_

__
**Ina gamawa na shige dakin Umma ina hawaye saboda abin inna Harira ya fara yi min yawa, bana san hantara na samu guri na kwanta. Umma ta shigo ta ganni sai faman turo baki nake, tayi murmushi kawai ta zauna kusa dani tana shafa kaina.

"Baki da lafiya ne?"

Ta tambayeni cike da kulawa. Nai narai-narai kamar zanyi kuka ina cewa.

"Umma bata sona."

"Waye baya sonki?"

"Inna Harira."

Cikin sauri ta kalli bakin kofa ganin babu kowa yasa ta kallona tana shafa gefen fuskata tace.

"Tana sanki karki sake cewa bata sanki idan taji sai tafi takura miki."

"Toh dagaske ne ni ba yar nan gidan bace?"

Ta kuma saurin rufe min baki alamar bata san ta dinga jin ina wannan maganar.

"Ki dena biyewa zancen ta so take taga kina kuka, bakiga yadda take yiwa su Fatsima ba? Suma ai ba kyalesu tayi ba ki dena damuwa kinji ko?"

Murmushi nayi sai naji dadi da kalamanta, Umma mutuniyar kirki ce, duk irin wulakanci da rashin mutunci da irin dibar albarkar da Inna Harira keyi mata tasan yadda zata zauna da ita, dan bata bari suyi rigima duk kankantar ta. 

Nan da nan sai na tashi na fita da gudu muka hadu dasu Indo aka ci gaba da wasa. Ana gama abinci aka bamu mukaci sai muka sa hijabai muka tafi makarantar allo, kafin la'asar muka koma gida mukai shirin islamiya sai da muka yi sallah muka tafi.

 Rayuwar mu haka take tafiya kullum tun tasowa ta a gidan duk munsan lokutan yin abubuwan mu.

Saboda Gwani Tsayyabu mutum ne jajirtacce akan duk wani al'amari nashi, baya san wasa akan sha'anin karatu musamman na addini, shi yasa duk muna haddar kur'ani a kan mu. Yana so yaga muna karatu sosai saboda yana yawan gaya mana cewa karatu shine mutum idan mutum bashi da ilimi wawa ne kuma dolo da bashi da alkibla.

Makaranta kuwa an kammala gina gabaki daya har an fitar da kalar uniform  Kullum kunnuwan mu duk sun bude jira kawai muke a ce ga ranar da zamu fara zuwa makaranta.

Wata rana an aikeni kai nika naje nakai sai mai injin yace dole sai na bari an tara da yawa sannan zai tada injin. Ni kuma dan karna koma gida inna Harira ta sani wani aikin yasa na koma karkashin bishiya ina yar carafke, akwai wani daga gefe zaune akan benci yana shan rake ya kirani.

"Ke zo nan."

Ina jinsa nai masa banza, ya sake kirana.

"Ke badake nake bane."

Na juya na kalleshi.

"Wai ni?"

"Eh ke, zoki karbi rake."

Na tashi da sauri na isa gurinshi, maimakon ya bani sai ya riko hannuna yana dariya tare da janyoni jikinsa nace.

"Sakarni."

"Bakya san raken? Ki tsaya baki zanyi."

Yana magana yana sake rikoni, ni kuma ina fizgewa, karshe dai dai ya matseni da kafa na fashe da kuka gashi babu mutane a wajan duk an tafi masallaci sallar la'asar.

"Ni ka sakeni, wallahi zan gayawa Umman mu, ka kyaleni bana san raken."

"Bazan sakeki ba, kuma idan baki min shiru ba sai na fasa miki baki yanzun nan."

Ganin ba zai kyaleni ba yasani cizansa a hannu amman be kyaleni ba sai ma kara matseni da yake yi. Sai da ya hango wasu mutane sun fara tahowa sannan ya sakeni ya tashi ya bar gurin da sauri. Suna karasowa suka gani ina kuka suka tambayeni nace musu wani ne ya gudu suka fara bani hakuri wani a gefe yana cewa.

"Be kamata dama a dinga barin yara mata suna yawan kai markade ko nika ba, gwara a samu ko almajiri ne ya dinga yin aiken."

Ina jin su nidai bance komai ba suka wuce ni kuma na koma inda nake naci gaba da wasana.

MASARAUTA (LABARIN SOYAYYAH) YANA AREWA BOOKS👇

https://arewabooks.com/book?id=6284e72eef85a63a21dbc5f5

SO DA ZUCIYA

SHIMA YANA AREWA BOOKS👇

https://arewabooks.com/book?id=623f824f9c4af77be0e96e3d

🥰😍
_ZAFAFA BIYAR!! ZAFAFA BIYAR!! ZAFAFA BIYAR!!_

_ASSALAMU ALAIKUN MASOYA MAKARANTA LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_

_BARKAN MU DA SALLAH, ALLAH YA MAIMAITA MANA, AAMIN_

_KU MATSO KUSA, ZAFAFAN NAKU SUN SAKE ZABUROWA DA ZAFIN SU KAMAR YADDA KUKE KAUNAR SU._

_WANNAN KARON MA SUNZO DA WANI SALO MAI NUTSUWA HADI DA ZAFAFAN DARUSSA NA RAYUWA KANA DA FADAKARWA AKAN RAYUWAR YAU.. BANGAREN KOGIN KAUNA KUWA BAA MAGANA. DOMIN WANNAN KARON SUN SAKE TAHOWA DA ZAFAFAN KAUNANNAKI MASU NARKE ZUCIYOYI._ WANDA ZASU ZO MUKU  IN SHA ALLAH 

_KADA KU MANTA ZAFAFAN NAKU DE SUNE KAMAR HAKA_

_SAFIYYAH HUGUMA: TAZO DA NATA SALON MAI SUNA: *KUFAR WUTA*_🥰

_BILLYN ABDULL TA ZABURO DA WANI TAKEN MAI SUNA: *BAQAR INUWA.*_😍

_MAMUH GEE ITAMA WANNAN KARON TA SAKE TAHOWA DA: *NOORUL-ALB*_🥰

_HAFSAT RANO WANNAN KARON TAZO DA NATA RUBUTUN MAI SUNA: *RAYUWAR MACE*_❣️

_NANA HAFSATU (MSS XOXO) WANNAN SALON MA TAZO DA : *MASARAUTA*_😍

***_DUKA LITTAFAI BIYAR ZASU ZO MUKU NE AKAN FARASHIN YADDA SUKE KAMAR KODA YAUSHE_*

_BIYAR : DUBU DAYA (1k)_
_HUDU: 700_
_UKU: 500_
_BIYU: 400_
_DAYA: 300_

_AKWAI TSARIN VVIP SUITES GA MASU SON HAKAN. FARASHIN SU DABAN, DOMIN KARIN BAYANI SE A TUNTUBE  MU TA: _

*_ZAKU BIYA KUDINKU ANAN👇👇_*

Bilkisu Ibrahim Musa
1487616276
Access bank

Number shaidar biya👇🏼

*_09032345899_*

*KATIN MTN*👇👇 

09166221261

YAN NIJAR 👇

+227 95 16 61 77

Ga 'yan nijer zasu tura katin moov ko Airtel zuwa wannan number
______________________

ZAFAFA BIYAR

VVIP SUITES : 3500 (PC/TA PRIVATE KAI DAYA)

VIP SUITES : 3K (VIA GROUP) A VIP GROUP ZAA DINGA TURAWA.

TWO PAGES DAILY
INSHA ALLAH!! MORNING/NIGHT. SAFE DA DARE.


*_TEAM ZAFAFABIYAR_*

_MSS XOXO WRITES ❣️_
[5/22, 9:58 PM] Miss Xoxo: _*MASARAUTA*_
_(A Cinderella story)_
           👑💘

   _FREE PAGE: 3_

_NA:_


®️ _NANA HAFSATU_

©️ _ZAFAFA BIYAR WRITERS_


_wattpad:missxoxo00_
_Arewabooks:mssxoxo_

_BUSINESS:👇🏾_

_YERWA INCENSE AND MORE: MASARAUTAR KAMSHI:_

_THE SCENTS WITH DIFFERENT ESSENCE FOR YOU AND YOUR HOME_

_DO YOU WANT THAT MAIDUGURI AND SUDANIAN SCENTS THAT LASTS LONGER AND LINGERS? YERWA INCENSE AND MORE GOT YOU AND YOUR BELOVED ONES COVERED WITH LUXURIOUS SCENTS. KAMSHIN YAN YERWA DA SUDAN💘🙏 20% OFF ORDERS. MUN CIRE KASO 20 NA KUDIN KAYAYYAKIN MU_

_KHUMRAHS_
_KULACCAMS_
_TURARUKAN WUTA_
_NA TSUGUNNO_
_NA KAYA_
_NA GIDAH_
_NA GASHI_

_NA WANKA_
_NA WANKI_
_NA MOPPING_

_AIR FRESHENER_
_CURTAIN AND CHAIRS SPRAY_
_WARDROBE BALLS_
_SCENTED PEBBLES_

_ARABIAN OIL PERFUMES_
_HAIR SPRAY AND CREAM_
_DILKE AND HALWA SET_

_KABBASA_
_BURNERS_
_KASKO_
_TONGS_
_COAL IGNITERS_

_SKIN CARE PRODUCTs_
_OUR TURARE SAMPLE SETS_
_BRIDAL SET (SAITIN AMARE)_
_KUJERAR TSUGUNNO_

_SABULAI NA GYARAN JIKI DA SAURAN KAYAYYAKIN GIDAH NA KAMSHI . KOMAI DA KOMAI AKAN FARASHIN SARI KO SAYI DAYA DAYA_

_MUNA TURA KAYAYYAKIN MU A KO’iINA A FADIN NIJERIYA DA KETARE_

_SIYAN NAGARI MAI DA KUDI GIDAH, 100% TESTED AND TRUSTED_

_instagram:yerwaincense_and_more_*

_WhatsApp: 08095215215_

*ENGLAND*
LEICESTER CITY TOWN OF LEICESTERSHIRE (EAST MIDLANDS)

**Zaune Haj Tasidi (Hafsat) take. Ta kifa kanta akan hannun kujera kirar royal. Kana kallon ta kasan ta lula duniyar tunani. Duba da yadda 'dan ta keta mata magana sam hankalinta baya jikinta. 

"Maaa.. "Ya sake fada da dan karfi. Damuwa shima ta sake lallube shi ganin yadda mahaifiyar su take. Ga ba ba mai cikakkiyar lapia ba. 

"Na'am.... " Ta amsa da sauri hade da juyawa .

Ganin Aliyu ne yasa ta danyi murmushi . 

 "Ka dawo?"

"Na dawo ba jimawa Maaa. Ya jikin na ki?"

"Jiki Alhamdulillah. Ga abinci can kan dinning. "

"Ban jima da ci ba a office, Sai dai ko anjima.  Papaa ya tashi kuwa?"

"Maganin ne yana da dan karfi . Baccin har yanzu be sake shi ba sai ya sake komawa."

"Allah de ya kara muku lapia da nisan kwana mai amfani, Aamin"

"Aaamin"

Ajiyar zuciya ta sauke mai nauyi, Aliyu dake gefenta ya dan sake sunkuyar da kansa . Ahankali cikin tattausar murya yace.

"Kiyi hakuri Maa, In Sha Allah. Karshen damuwar mu ya kusa zuwa karshe. Tunda an tabbatar da h..."

Daga masa hannu tayi alamun yayi shiru. Hannunta daya na kan setin zuciyar ta. Ji take tamkar zuciar tata zata faso ta fado kasa. Saboda tsabar yadda gabanta ya tsananta bugawa. 

"Hasbun Allahu wa ni'imal wakil. ." Ta furta ahankali tana mai dartse kasan lebenta 

Ganin haka yasa Aliyu tashi ahankali yayi dakin mahafinsu dake kan gado ba lapia .....

**YANKIN KINDAU**


Murna taki barin cikin raina, zuciyata banda dadi da wani shauki babu abinda takeyi, ganin Allah yayi nima zanyi makaranta. A rayuwa ta ina so na ganni cikin uniform saboda ko a jikin wasu na gani sai naji wani farin ciki. Gashi muma yanzu za'a yi mana makaranta kamar yadda sauran yara masu galihu suke zuwa. Har wajan da ake tara kasa naje inda ire-irena suke wajan suna ta wasa akai, hauwa nayi nima ina ta tsalle tare da juyi.

Isowar Wasila wajan ya sake faranta min, na sauka da gudu naje muka rungume juna muna ihun dadi. Wasila ta sakeni tana kallona tace.

"Intee kema Babanku ya baki? Ni Kinga innar mu tace ko ana ha maza ha mata sai nayi saboda tana so nima na zama malama wata rana."

 Nima na washe baki ina lumshe ido irin na firiritar nan na ce da ita.

"Tun yaushe ya yarda, Ai dama cewa yake inde Allah yasa muna da rabon yin boko,  cewa yai ma sai nayi na samu aiki indai karatu ne."

 Muka sake rungume juna cike da farin ciki kafin mu hau kan yashin muma.

Bamu bar gurin ba har sai da aka kira magariba, shi din ma sai da wani mutumi ya kore mu dukan mu yaran wajan. Muna zuwa wajan gidan su Wasila ta shige ni kuma na fara tafiya ina ta kallan yadda wani Dattijo ya sauke mai farantin tsire ana ta zuge masa a cikin takarda. Caraf naji an kamo min dan karamin hijab din jikina, nai saurin daga kai ina kallan ko wanene, ganin Adamcy yasa na turo baki cikin bacin rai nace dashi.

"Allah Adamcy idan kana cewa zaka aureni sai na gayawa malam, ni karka sake cewa dani zakai soyayya." Sai ya sakeni ya fara dariya yana cewa.

"Haba Intee, taya za'a ce kina kyakkyawar nan baki da masoya irina? Ni zan aureki na mallaka miki shanu uku kiyi ta kiyo kina samun kudin." 

Na kuma turo baki.

"Allah idan ka sake cewa zaka aure ni Allah ya saka min." Sai ya sake kallo na yaga idanuna yana kan mai tsire, hakan yasa shi yin murmushi tare da cewa.

"Idan kika yarda zaki aureni yanzu muje na sai miki tsire tsinke biyu." Nayi shiru ina tunani gashi yawuna ya biya da tsiran, na kama kugu tare da kallanshi cikin ido nace.

"Banaci tunda ni ba mayya bace, aure kuma in ka sake cewa kana sona wallahi sai na gayawa Baban mu."

 Adamcy ya toshe baki da hannunsa yana zaro ido cike da mamakin abinda nace.

Juyawa nai na tafi cike da jin haushi. Ina shiga na tarar an zuzzubawa su Fatsima tuwo nima naje gurin Umma na karbo nawa na samu guri a tsakar gida na zauna, ana ci ana surutu kuma duk akan ginin makarantar da za'ayi manane. Sai da mukaci muka koshi sannan kowa yaje ya dauki bjta yai alwala, nima nayo tawa naje nai sallah daga nan sai makarantar dare, a can muka yi isha'i sai karfe tara na dare muka dawo gida duk da cewa makarantar a kofar gida ce dan ta Babace.

Tsabar sanya makarantar a raina har mafarki nayi da ita, na ganni ina ta zuba kokari duk abinda akai nice nake fara iyawa. Sai da naji Umma na tashina sallar asubahi sannan ne na tabbatar da cewa mafarki nayi ba wai da gaske bane ba. Bayan munyi sallah makarantar asuba mukaje sai karfe takwas muka koma gida akayi karin kumallo daga nan sai debo ruwa, muna gamawa mukai wanka akai aiki wadanda suka yi da wuri ni da Fatsima da bamu gama da wuri ba aka samu dake-daken abubuwan da za'a dora girki.

Duk da irin karancin shekaru da nake dasu, dan a lokacin shekaruna tara a duniya, hakan be hanani gane irin yadda Inna Harira ke nuna banbanci tsakanina da sauran yaran gidan ba, ko abu indai itace zata raba sai nawa yafi na kowa kankanta, idan nai magana ta bubbuge min baki ko ta rankwashe ni tace na mata sharri ko tace haka taga damar bani idan ina da karfi nazo na kwata.

Ni kuma duk lokacin da tai min haka sai naji girmanta da darajarta sun zube a cikin raina. Muna zaune bayan mun gama jajjagen kayan miya kawai Inna Harira ta kalleni, gashi rana ta fara budewa ta cillo min tsintsiyar kwakwa tana cewa.

"Tashi ki share gidan nan gayan bishiya duk ya sake batashi." Cikin turo baki tare da langabewa dan ta tausaya min nace.

"Inna Harira Kinga rana fa.?"

 Tace dani.

"Eh wallahi na ganta sai akai me?"

 Nace.

"Dan Allah ki bari zuwa la'asar sai nayi." 

Sai cewa tayi.

"Iyeee! Lallai yarinyar nan, ince kiyi abu yanzu ki tsaya kina zabar lokacin da zaki yi? Toh yanzu nace kuma sai kinyi kodan wannan hasken naki ya ragu, yarinya abinda kowa yakeci shi kike dankara amman kinfi uban kowa haske a gidan nan? Toh yanzu zaki share gidan nan idan kuma kinki zakisha mamaki."

Sai bance komai ba na tashi ina kunkuni na fara sharewa kamar zan fashe da kuka....

MASARAUTA (LABARIN SOYAYYAH) YANA AREWA BOOKS👇

https://arewabooks.com/book?id=6284e72eef85a63a21dbc5f5

SO DA ZUCIYA

SHIMA YANA AREWA BOOKS👇

https://arewabooks.com/book?id=623f824f9c4af77be0e96e3d

🥰😍
_ZAFAFA BIYAR!! ZAFAFA BIYAR!! ZAFAFA BIYAR!!_

_ASSALAMU ALAIKUN MASOYA MAKARANTA LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_

_BARKAN MU DA SALLAH, ALLAH YA MAIMAITA MANA, AAMIN_

_KU MATSO KUSA, ZAFAFAN NAKU SUN SAKE ZABUROWA DA ZAFIN SU KAMAR YADDA KUKE KAUNAR SU._

_WANNAN KARON MA SUNZO DA WANI SALO MAI NUTSUWA HADI DA ZAFAFAN DARUSSA NA RAYUWA KANA DA FADAKARWA AKAN RAYUWAR YAU.. BANGAREN KOGIN KAUNA KUWA BAA MAGANA. DOMIN WANNAN KARON SUN SAKE TAHOWA DA ZAFAFAN KAUNANNAKI MASU NARKE ZUCIYOYI._ WANDA ZASU ZO MUKU  IN SHA ALLAH 

_KADA KU MANTA ZAFAFAN NAKU DE SUNE KAMAR HAKA_

_SAFIYYAH HUGUMA: TAZO DA NATA SALON MAI SUNA: *KUFAR WUTA*_🥰

_BILLYN ABDULL TA ZABURO DA WANI TAKEN MAI SUNA: *BAQAR INUWA.*_😍

_MAMUH GEE ITAMA WANNAN KARON TA SAKE TAHOWA DA: *NOORUL-ALB*_🥰

_HAFSAT RANO WANNAN KARON TAZO DA NATA RUBUTUN MAI SUNA: *RAYUWAR MACE*_❣️

_NANA HAFSATU (MSS XOXO) WANNAN SALON MA TAZO DA : *MASARAUTA*_😍

***_DUKA LITTAFAI BIYAR ZASU ZO MUKU NE AKAN FARASHIN YADDA SUKE KAMAR KODA YAUSHE_*

_BIYAR : DUBU DAYA (1k)_
_HUDU: 700_
_UKU: 500_
_BIYU: 400_
_DAYA: 300_

_AKWAI TSARIN VVIP SUITES GA MASU SON HAKAN. FARASHIN SU DABAN, DOMIN KARIN BAYANI SE A TUNTUBE  MU TA: _

*_ZAKU BIYA KUDINKU ANAN👇👇_*

Bilkisu Ibrahim Musa
1487616276
Access bank

Number shaidar biya👇🏼

*_09032345899_*

*KATIN MTN*👇👇 

09166221261

YAN NIJAR 👇

+227 95 16 61 77

Ga 'yan nijer zasu tura katin moov ko Airtel zuwa wannan number
______________________

ZAFAFA BIYAR

VVIP SUITES : 3500 (PC/TA PRIVATE KAI DAYA)

VIP SUITES : 3K (VIA GROUP) A VIP GROUP ZAA DINGA TURAWA.

TWO PAGES DAILY
INSHA ALLAH!! MORNING/NIGHT. SAFE DA DARE.


*_TEAM ZAFAFABIYAR_*

_MSS XOXO WRITES ❣️_
[5/22, 9:58 PM] Miss Xoxo: _*MASARAUTA*_
_(A Cinderella story)_
           👑💘

   _LAST FREE PAGE: 5_
_(shafin karshe na kyauta)_

_NA:_


®️ _NANA HAFSATU_

©️ _ZAFAFA BIYAR WRITERS_


_wattpad:missxoxo00_
_Arewabooks:mssxoxo_

_BUSINESS:👇🏾_

_YERWA INCENSE AND MORE: MASARAUTAR KAMSHI:_

_THE SCENTS WITH DIFFERENT ESSENCE FOR YOU AND YOUR HOME_

_DO YOU WANT THAT MAIDUGURI AND SUDANIAN SCENTS THAT LASTS LONGER AND LINGERS? YERWA INCENSE AND MORE GOT YOU AND YOUR BELOVED ONES COVERED WITH LUXURIOUS SCENTS. KAMSHIN YAN YERWA DA SUDAN💘🙏 20% OFF ORDERS. MUN CIRE KASO 20 NA KUDIN KAYAYYAKIN MU_

_KHUMRAHS_
_KULACCAMS_
_TURARUKAN WUTA_
_NA TSUGUNNO_
_NA KAYA_
_NA GIDAH_
_NA GASHI_

_NA WANKA_
_NA WANKI_
_NA MOPPING_

_AIR FRESHENER_
_CURTAIN AND CHAIRS SPRAY_
_WARDROBE BALLS_
_SCENTED PEBBLES_

_ARABIAN OIL PERFUMES_
_HAIR SPRAY AND CREAM_
_DILKE AND HALWA SET_

_KABBASA_
_BURNERS_
_KASKO_
_TONGS_
_COAL IGNITERS_

_SKIN CARE PRODUCTs_
_OUR TURARE SAMPLE SETS_
_BRIDAL SET (SAITIN AMARE)_
_KUJERAR TSUGUNNO_

_SABULAI NA GYARAN JIKI DA SAURAN KAYAYYAKIN GIDAH NA KAMSHI . KOMAI DA KOMAI AKAN FARASHIN SARI KO SAYI DAYA DAYA_

_MUNA TURA KAYAYYAKIN MU A KO’iINA A FADIN NIJERIYA DA KETARE_

_SIYAN NAGARI MAI DA KUDI GIDAH, 100% TESTED AND TRUSTED_

_instagram:yerwaincense_and_more_*

_WhatsApp: 08095215215_

__

**Da sassafe na tafi kogin Guzai ebo ruwa da wanka, Kasancewar kogin Bagaja ya kafe. Ba wani layi sosai . Mutane uku ne agabana. Don haka na zauna akan bokiti na ina rufe baki na da hammar data tahomin. 

Sai dana cika babban bokiti na. Na ajiye a gefe, Tukun sannan na ebo wani a bokitin wanka. Na tsaya can bayan bishiyar darbejiya inda muke wanka wani sa'ilin. 

Wanka na na fyalla na dauraye gashi na da guntun omon da muke wanke kai da shi. Ni kai na mamakin yawan gashi na nake, Ga cika ga tsayi. Dan basilin din dana lakato a leda na dakko na shafe a jiki na. 

Na zura kayana. Na koma bakin kogi na daura gammo na dasa ruwana a kai. Dayan bokitin kuma na dauke shi a hannu. Ina tafe ina bitar karatu na. 

***Na baro kogin Guzai gaba ki daya so nake na koma gidah saboda yadda cikina yafara kukan yunwa.

Can sai Adamcy da Nazifi da suke kira da Nazicy. Dake duk yuyar abokan nasu sun mayar da sunayen da cy a karshe tamkar wasu arna.

Yana gani na ya dashe hakora. Tsabar sauri har tuntube na danyi ruwana ya zubo. Domin sam banason su tsayar da ni.

"Tawaje na....Masoyiyar."

Ban kula shi ba nayi gaba. Amma tsabar nacin sa sai ya sake biyo ni yana kobarewa. Ya saka hannuwan sa ya dauke bokitin da ke kai na ya rike.

"Bani ruwana.." Na fada wani hawaye na son kufcemun. 

"Haba tawaje na. Saboda me zan bar ki ki dauki sungumemen bokitin nan bayan gani da rai na. "

Hawayen da nake rikewa kar ya zubon suka fara yar tsere a fuskata. 

"Adamcy dan Allah ka kyaleni."

"Saboda me zan kyale ki bayan kin san kaunar ki nake da aure...?"

"Aure?" Na fada murya ta a kausace saboda 'dacin maganar da yamun 

"Eh aure... "

Na girgiza kai kawai Ina mai busar da iskar baki na mai zafi da radadin yadda ya fada a gadarance.

"To Adamcy bazan aure ka ba. Idan auren kakeso. Kaje ka auro budurwa babba mana. Ga su luba nan ta hayin dusa, Ga Rabi nan ta yan koko dasu sha'awanatu ta gidan wake da shinkafa..ga"

"Karki karasa Intee, Ni ke nagani inaso, Kuma ke zan aura koda kuwa zan rasa kowa da komai nawa."

Takaicin kalamansa yasa naja dogon tsaki. Na kwararo dogayen rantsuwa na dire hade da bubbuga kafafuna a kasa.

"To ka kwana da sanin ni Inteesar bazan yi soyayyah da kai ba don ni ba budurwa ba ce da har zanyi wani saurayi yanzu bare aure. Shekaru na dududu nawa a duniya eh? Nace nawa? Karatu zanyi insha Allah. yadda MASARAUTA ta temake mu zata debi yara mata suyi karatu haka zanyi insha Allah. Kama cire ni...."

Ajiye bokitin Adamcy yay a kasa. Ya shafa gashin sa daya shafa masa kunfan los yayi 'dai dai dashi kamar wani mace. Tsakiyar gashin yasa matajin kai acikin sa  Ya sake dedeta tsayuwar sa. Yana mai jan kasan leben sa.

"Ni Adamcy dan gidan Alhaji zakiwa haka? Duk yankin kindau akwai wanda ubansa yaje makka bayan nawa uban? Kaf garin nan wakeda shagon kayan masarufi idan ba Alhajin mu ba? Ko kuwa kunada injin dake baku wuta? Shanu 'dai dai har nawa nace zan baki idan kika amince zaki aure ni? Eh? Ki ajiye wauta a gefe kidubi zahiri, Shayi da burodi sekin gaji da shi Intee, Indomin ukasha da tsiren tanimu sekin ture, zuwa cikin birni duk sati na miki alkawarin nan zamu dinga zuwa hutawa. Akwai gidan kawu na acan.."

Dogon tsaki naja. Na sauke ajiyar zucia kawai. 

"Adamu bazan yi soyayya da kai ba, Ballantana aure ya shiga tsakani na da kai.. Ai bani kadai ce mace a kindau ba. Na kuma gode da kaunar da ka nuna mun. Allah ya baka wata ta gari Amin."

Ban tsaya jin tacewar sa ba, Nayi gaba abuna bayan na sunkuce bokiti na. Nan na barshi a tsaye na tabbata mamakin kalamai na yake. Ni kuwa zucia ta fes . Nayi gaba abuna, inata Allah Allah sha biyun rana tayi muje kofar gidan hakimi a raba mana kayan makaranta. 


*NEWYORK CITY*
(Manhattan: Borough of Newyork)

  "Kai Nasser tashi ka kira yayan ku, wallahi idan mukayi missing flight sai ransa ya 'baci."

Haj zaynab ta dubi Nasser dan ta. Dake zaune kan hannun kujera yana latsa wayar hannun sa.

"Mami.. Wallahi banason ya hau ni da fada."

"Zaka tashi kaje ka gaya masa ko kuwa sai na saba maka?"

Ba yadda Nasser ya iya, Adole ya mike, Ya shiga haura matattakar benen, gaban sa na tsananta buguwa saboda yasan masifar halin yayan nasu."

"Knock knock"
Ya furta hade da kwankwasa kofar dakin.

"Yes! Who's there?"

"Itz Nasser! Mami tace kazo mu tafi kar muyi missing f...." Ai be karasa fada ba, yaja baya da sauri jin yadda yayan nasu ya jefo wani abu ta kofar. Ji kake gwararam gwam. 

Ai kuwa sum-sum-sum Nasser ya sakko da sauri yana sosa keya.

"Yana zuwa wai."

"Ai ba kurma bace na jiyo sautin bugo kofar da yayi ai. Uban yan bak'ar zuciya kawai. Allah ya shirya"

"Aamin!" Nasser ya amsa ahankali hade da juyawa baya gudun kar yayan nasu ya taho ya jiyo shi...

   ××Shi kuwa Mukhtar yana zaune a gefen gado. Ya gama hada kayan sa a akwati. Bakin ciki ne fal cikin zuciar sa na komawa rayuwar cikin MASARAUTA da zeyi. Bayan tsananin tsanar da yayi mata. 

Takanas mahaifin su yasa mahaifiyar tasu Haj zaynab taje tataho da Nasser din daga Newyork city. Da anan gabaki daya suke da zama. Bayan an masa kira kan yazo ya karbu mulki kuma gabaki daya iyalin sai suka koma kasar ta Nigeria. Mukhtar dinne kadai bai koma ba yace sai ya gama degree . Kuma yace ze dora da masters baban yace bai san zance ba. Sai ya fara zuwa MASARAUTA tukun ya zauna dasu na wani dan lokaci. 

Ajiyar zuciya ya sauke, Ya rufe akwatin nasa ya bi dakin da kallo kafin ya fuce ya sauka kasa. Ransa a matukar b'ace... 

Already sun shiga mota dama suna jiran sa, Sai daya mula ya sha iska tukun sannan ya wuce parking port. Ya shiga mota suka dauki hanyar airport don komawa kasar su ta gado wato Nigeria.....

--------------

Dankari makari!! ××Duka Duka anan free pages suka dakata. Labari ze cigaba daga kan paid pages (page 6) insha Allah . Shin wacece Inteesar? Meye usulinta? 

Kada ku manta ainihin gundarin labarin na ga MASARAUTA! Wanda anan ne zaa baje muku kolin labarin. 

MASARAUTA labarine daya tabo rassa da dama. Wanda jigo babba na cikin labarin na akan sadaukarwar SOYAYYAH. Ita SOYAYYAH za ka iya sadaukar da komai akanta don samun mallakarta. 

Abubuwa da dama na dauke acikin LITTAFIN masarautar. Wanda iya Wanda suka siya ne kawai ke da damar karanta shi. 

Kuzo a dama da ku don yanzu tafiyar zata soma.

Kada ku manta. Zafafan naku biyar de. 1k ne pages. Vip 3k, vvip 3500.

Ga masu son a musu tallan hajojin su. Duka seku tuntube mu akan payment details dinmu dake kasa👇

MASARAUTA (LABARIN SOYAYYAH) YANA AREWA BOOKS👇

https://arewabooks.com/book?id=6284e72eef85a63a21dbc5f5

SO DA ZUCIYA

SHIMA YANA AREWA BOOKS👇

https://arewabooks.com/book?id=623f824f9c4af77be0e96e3d

🥰😍
_ZAFAFA BIYAR!! ZAFAFA BIYAR!! ZAFAFA BIYAR!!_

_ASSALAMU ALAIKUN MASOYA MAKARANTA LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_

_BARKAN MU DA SALLAH, ALLAH YA MAIMAITA MANA, AAMIN_

_KU MATSO KUSA, ZAFAFAN NAKU SUN SAKE ZABUROWA DA ZAFIN SU KAMAR YADDA KUKE KAUNAR SU._

_WANNAN KARON MA SUNZO DA WANI SALO MAI NUTSUWA HADI DA ZAFAFAN DARUSSA NA RAYUWA KANA DA FADAKARWA AKAN RAYUWAR YAU.. BANGAREN KOGIN KAUNA KUWA BAA MAGANA. DOMIN WANNAN KARON SUN SAKE TAHOWA DA ZAFAFAN KAUNANNAKI MASU NARKE ZUCIYOYI._ WANDA ZASU ZO MUKU  IN SHA ALLAH 

_KADA KU MANTA ZAFAFAN NAKU DE SUNE KAMAR HAKA_

_SAFIYYAH HUGUMA: TAZO DA NATA SALON MAI SUNA: *KUFAR WUTA*_🥰

_BILLYN ABDULL TA ZABURO DA WANI TAKEN MAI SUNA: *BAQAR INUWA.*_😍

_MAMUH GEE ITAMA WANNAN KARON TA SAKE TAHOWA DA: *NOORUL-ALB*_🥰

_HAFSAT RANO WANNAN KARON TAZO DA NATA RUBUTUN MAI SUNA: *RAYUWAR MACE*_❣️

_NANA HAFSATU (MSS XOXO) WANNAN SALON MA TAZO DA : *MASARAUTA*_😍

***_DUKA LITTAFAI BIYAR ZASU ZO MUKU NE AKAN FARASHIN YADDA SUKE KAMAR KODA YAUSHE_*

_BIYAR : DUBU DAYA (1k)_
_HUDU: 700_
_UKU: 500_
_BIYU: 400_
_DAYA: 300_

_AKWAI TSARIN VVIP SUITES GA MASU SON HAKAN. FARASHIN SU DABAN, DOMIN KARIN BAYANI SE A TUNTUBE  MU TA: _

*_ZAKU BIYA KUDINKU ANAN👇👇_*

Bilkisu Ibrahim Musa
1487616276
Access bank

Number shaidar biya👇🏼

*_09032345899_*

*KATIN MTN*👇👇 

09166221261

YAN NIJAR 👇

+227 95 16 61 77

Ga 'yan nijer zasu tura katin moov ko Airtel zuwa wannan number
______________________

ZAFAFA BIYAR

VVIP SUITES : 3500 (PC/TA PRIVATE KAI DAYA)

VIP SUITES : 3K (VIA GROUP) A VIP GROUP ZAA DINGA TURAWA.

TWO PAGES DAILY
INSHA ALLAH!! MORNING/NIGHT. SAFE DA DARE.


*_TEAM ZAFAFABIYAR_*

_MSS XOXO WRITES ❣️_
