[6/24, 9:46 AM] +234 701 013 7848: Fikrah writers association  *MAFARI* .....               ( _HARGITSIN RAYUWA_ ) *Umm'muaz*        بِسْــــــــــــــــمِ اللَّهِ الرَّحْمَ الرَّحِيْم....... *In The Name Of Allah, The Beneficent, The Merciful.* *Da Sunan Allah Mai rahama Mai Jinƙai* .    _MAFARI...komai yana da farko, komai yana da tushe, komai yana da asali, HARGITSIN RAYUWA kan faru cikin kankanin lokaci_ . _Duniyar daka saba da ita zata iya birkicewa zuwa baquwa a gareka cikin kankanin lokaci._ _Tafiya mabanbanciya da sauri, a cikin kaddara da dai-daito._               1 *SHIMFIƊA* Ƙauyen Mairambiri , wani ƙauye ne , ko kuwa "ƙaramar Alƙarya" da yake tsakanin ƙananan  hukumomin bama da konduga, wanda suke a karkashin jahar  ( BORNO ) Mutanen garin mafi akasarin su barebari ne " kanurai", sai kuma shuwa, da fulani, tsilla-tsilla, babbar sana'ar mutanen garin shine noma, suna da makarantun primary da secondry na gomnati, sai  kuma makarantun allo da mafiya yawan yaran garin  shi suka fi zuwa ,tsiraru ne suke zuwa bokon da suke kira karatun "Malam nasara", kasancewar garin nasu yana tsakanin manyan-manyan hukumomi biyu ya sanya suke da kasuwar su a bakin babban titin da yake tsakanin garin bama da konduga" wacce take ci duk ranar Alhamis.                        ************** Cikin wani ƙwarababben gidan kasa , wasu yara ne su uku mata,  suna cin wani zazzafan damalmalallen tuwon hatsi miyar kuka shar cikin wani tsohon kwanon da duk lamba da tsatsa suka gama munana shi , babbar baza ta wuce shekaru 16 ba ,sai ta tsakiyar me kimanin shekaru 14, sai kuma ƙaramar su me kimanin shekaru 8. Cikin nutsuwa babbar ta ke kai lomar tuwon bakin ta bayan ta sanyawa ƙaramar su ita ma a bakin ta ,saboda zafin tuwon ta kasa sanya hannu taci ,"alama yanzu aka sauke dumamen tuwon daga wuta "duk da yanzun farar safiya ne ko 6:30am bai cika ba. Wata doguwar mace siririya me ɗauke da wata irin farar fata sol-sol kamar ta so ta zama zabiya " Albinism" dan hasken ta yayi irin nasu, wacce da ganin ramar da take da shi na tsabar wahala da talauci ne ,tana zaune kofar wani taƙwarƙwasashiyar rumfa da alama madafi ne ganin yadda duhun wajen yafi na ko'ina a gidan, hannunta riƙe da wani jariri namiji kansa tanƙwal da aski , ta ciro yamushashen siririn maman ta tana kokarin cusawa yaron a baki shi kuma daga ya kama yayi tsotsa ɗaya-biyu yake sakewa ya cigaba da tsala kukan da yake da alamun yunwa ce ke addabar sa . Wani baƙin dogon mutum ne, ya bullo daga bayan durkusassun ɗakunan nasu guda biyu ,hannun sa rike da babbar robar ruwa (table water ), wacce aka yanke daga wuyan ta zuwa sama gefen ta daga kasa yana ɗan ɗigar da ruwan ciki daidai inda ya ɓule aka toshe da bakar leda . Duƙawa  yayi tare da   wanke baƙaƙen kafafuwan sa da suke sanye cikin waɗansu ratattakakkun silifa (da guntun ruwan )  ,ya ɗago tare da kallon sashin da ƴaran nan suke zaune ya ɗan ɗauki wasu daƙiƙai yana kallon su cikin nazarin yadda babbar cikin take ta ciyar da kannan nata domin ya zuwa yanzu dai su duka biyun ita take sanya hannu tana zaƙulo tuwon da ya dilmiye cikin tsululun ruwan miyar da ta haura tuwon yawa har ta shaa kansa ,tana zaƙulo shi sannan ta hura iskar bakin ta ta gutsurawa ɗayar a hannu ta sanyawa karamar sauran abakin ta , kuma a take ta sake mayar da hannun ta cikin kwanon da hanzari tamkar dai ita bata jin zafin tuwon . Yakaka " _nyidin biri bun" baa ? Duwan "bii lanyen wande kausuzuin_ (yakaka ke baza ki ci abincin bane ? Kiyi sauri ki ci mu tafi kar rana ta yi ) cewar wannan mutumin ga babbar ɗiyar ta sa da ya kira da suna yakaka cikin yaren su na " _KANURI_ . Amsa masa tayi da "toh" ,dai-dai lokacin da ta miƙe da hanzari ta zagaya ta bayan matar nan da hasken fatar su yake yanayi ɗaya da nata ,ta ɗauko wani bakikkirin ɗin tiren kwano da yayi fatsa-fatsa da lamba ta nufi fasashiyar randar su da take binne a kasa sai iya fasashen bakin ta ake gani a waje "wanda za'a iya zaton rami ne"  ta sunkuya tayi goho ta kwarfi ruwa a chan kasa ta ɗauraye farantin , Ta sake kwarfo wani  ruwan a cikin bulalliyar moɗar da ta sha liki da leda , cikin gudu gudu ta je ta juye tuwon a kan farantin tare da ajiye musu ruwan , har ta yunƙura ta tashi ,sai karamar ta riƙo hannun ta ,a hankali ta ɗago idanun ta ta dubi kanwar tata wacce idan aka dauke kamanni irin na jini , da kuma siraran zane ( _Shunkurai_ ) da yake kan fuskokin su guda tara-tara "wanda yake bayyanawa a sarari daga ƙabilar da suke na barebarin usul " bayan hakan kowaccen su kamannin ta daban ne , Babbar su tana ɗiban yanayi da uwar su "watau fara ce sol yanayin hasken mutanen da suka so zama Zabiya ( albino ) yayin da ta tsakiyar take da rangwamen hasken fata ,karamar kuwa baka ce sosai kamar mahaifin su , Da alamu dukkanin su dogaye ne samɓala-Samɓala duk da cewa suna kan shekarun kuruciya sosai "yara ne " . Cikin yaren su  karamar ta cewa babbar ta kawo mata gurji daga gona, shafa kan ta  tayi cikin nuna kauna tace zata kawo mata daga haka ta juya ta nufi ɗakin su tare da sako wani ɗangalallen hijabi cukurkuɗaɗɗe yagagge bakikkirin da shi ta kuma zagaya bayan ɗakunan nasu ta ɗauko wani buhu da alama abubuwan bukata a gona ne a ciki. Duk abun da ake mahaifiyar  su  tana zaune bata umm "bata a ah ,sai faman girgiza jaririn ta take da sigar lallashi "shima fari ne sol irin ta amma  ita fuskar ta babu zane irin na ƴaƴan ta ga alamu ita ba babarbari bace , kamar yadda yaran da mahaifin su kana kallon fuskar su zaka shaida yaren su . Sun zo zasu fita ita da mahaifin su  mahaifiyar  su ta miƙe ta rako su bakin zubabbiyar katangar da baza'a  ce mutane na rayuwa cikin zagayen ta ba , a bakin labulen tsunman da aka kare wawakeken giɓin da ya kasance mashigar gidan ( ƙofa ) , ta tokare sannan ta ɗaga hannu cikin maganar kurame tana musu alamar a dawo lafiya ta hanyar jujjuya tafufukan hannun ta ( _bye-bye_ ) tare da yin gwalatu cikin maganar bebaye," wanda hakan shi yake bada tabbacin KURMA ce "kallo ta bisu da shi fuskar ta ɗauke da murmushin da sai ita kadai ta san dalilin yin sa a cikin wannan yanayin da su ke ciki" . Sun dauki tsawon lokaci suna girbi cikin ƙatuwar gonar su da take wajen gari ,Suna hirar su da kana ji kasan akwai soyayya da shaƙuwa me karfi tsakanin uban da ƴar sa kafin lokacin da yakaka ta cewa mahaifin su zata je kama ruwa (Ban ɗaki )  , ta juya gami da shiga cikin dogayen shukokin masarar da suka fidda kai suna jiran girbi , tana tsugunne cikin duhun gonar ta fara jiyo kabbara tare da iface-ifacen mutane . Ta miƙe da sauri tana sanya ɗan kanfai (wondon ta ) , lokacin da taji mahaifin ta yana kwala kiran  neman ta da sauri ta nufo wurin da taji muryar sa , ita ma ta buɗe murya tana kiran sa tare da shaida masa ta dai-dai wurin take , wata razananniyar karar da taji tare da sake kusantowar kabbara da hayaniyar mutanen nan shi ya sake sa ta ruɗe . Duk da bata san bindiga ba a zahiri amma tasan karar nan da take ji na abu me cutarwa ne , har zuwa lokacin da taji muryar mahaifin ta cikin ƙaraji yana cewa ta kwanta kar harbin bindiga ya same ta , ai sai ta sake ruɗewa ta nufo inda ta ji muryar sa cikin gunjin kuka da kiran sunan sa . Shi kuma jin ta nufo shi ya sanya ya miƙe daga kwanciyar da yayi dan gujewa harsashi ,ya nufi inda yake jin kukan ta cikin tsoron kar harsashi ya same ta ko kuma ƴan tawayen su ganta su harbe ta ko su tafi da ita ( kamar yadda suka samu labarin hakan na faruwa a sauran garuruwa da ƙauyukan borno *ƳAN TAWAYEN BOKO HARAM* sun addabi mutanen ƴankin arewacin nigeria musamman jahar Borno da kewayenta wanda a nan mafarin abun ya ke. ) yana miƙewa yayi taku ɗaya biyu a na uku yaji kamar wani abu me karfi ya wuce ta jikin sa ya ɗauke shi yayi jifa da shi , yaji jikin sa kamar ba nashi ba . Dai-dai lokacin da Yakaka ta ci tintiɓe da shi da sauri ta sunkuya gami da kamo shi ihun da ya ga ta sa tare da daura hannun ta akan kirjin sa yaga ta ɗago hannun na ta face-face da jini, shi ya tabbatar masa cewa harsashi ne ya same shi ,a take ya fara salati da karanto ɗukkanin addu'o'in da suka zo kan sa a lokacin  . Ita da kanta baza ta iya kiyasta tsawon lokacin da ta ɗauka a zaune rungume da gawar mahaifin nata , wanda tun bayan da harsashin ya same shi bai sake ko minti goma ba ya rasu . ( *Yaa Allah ya jikan dukkanin ƴan uwa musulmai da suka rasa rayukan su a sanadin annobar Boko haram Ameen* ) Tayi kuka har hawayen ta ya ƙafe har tunanin ta ya tsaya , ta gigice iyakar ɗimaucewa ,ta rasa hankalin ta a tsakiyar gonar rungume da gawar mahaifin ta wanda jinin sa ya bata mata jiki face face ,har wani wuri ya fara bushewa a hankali ta ɗaga kanta ta dubi yadda dare ya fara alamun shigowa rana ta tafi zata faɗi ga kuma  hadarin da yake haɗowa, cikin shishiƙar kuka ,jiri da tsananin galabaita ta ɗaga kan mahaifin nata da tun kafin rai ya kammala fita daga jikin sa ta ɗora kan sa a kan cinyoyin ta a gaban idanun ta ya rasu ,ita ta ke bashi kalmar shahada duk da karancin shekarun ta , cikin wani irin kuka ta sake mayar da kan nashi ta ajiye bisa cinyoyin nata tare da sake rungume gawar shi ( da ta Riga ta fara ƙandarewa ) tana wani irin shishikar kuka , ta ɗau tsawon lokaci a haka sannan ta sake ɗagowa tare da zare hijabin kan ta ,ta shimfiɗa cikin karfin zuciya ta sauke kansa a hankali daga jikin ta ta ɗora akan hijabin nata, kuma ta ɗauki lokaci tana yi masa addu'a. Sannan ta mike a zabure ta juya cikin hanzari ta nufi hanyar gidan su domin ta sanar tana tafe tana waiwayen duhun ciyawar da ta riga ta kare gawar mahaifin nata , har dai  ta zura da gudu tana kuka tana sharar hawayen ta. Birki ta jaa tare da rage takun tafiyar ta lokacin da ta bullo bakin hanya , hakan yana da nasaba da guje guje gami da iface-iface da ƙarar harbe-harben da take ji yana tashi daga ainahin cikin ƙauyen nasu , kowa ta nufa da gudu domin ta tsaida shi tayi tambayar me ke faruwa sai taga an bangaje ta an wuce da gudu wasu na kuka wasu na salati da addu'o'i wasu kuwa kana ganin su ma kasan gudun ceton rayukan su suke domin dai duk sun kukkuje sun ji munanan raunika ,amma ahaka suke gudu suna barin ainahin cikin ƙauyen nasu zuwa cikin gonaki da daji. A hankali ta ɗaga kanta sama tana iya hango yadda sararin samaniyar ƙauyen nasu ya tuniƙe da hayaki har ma tana iya hango harshen wuta da yayi tsiri yake toroƙo a wasu sashi na cikin garin, nan take wani irin tsoro da tashin hankali ya mamaye zuciyar ta tunowa da mahaifiyar da kannen ta da tayi suna cikin ƙauyen nasu ,da yanzu take hango tarwatsewar sa da mummunan bala'in da ya fada musu . Cikin karfin zuciya ta yunƙura da gudu ta nufi hanyar gidan su , tana ta cin gware da karo da mutanen da suke gudu daga cikin garin( amma ko kula bata yi  ba) zuwa lokacin da ta ji carafa an kama hannun ta da karfi an fusgo ta, da sauri ta waiwaya tana fatan  ko ɗaya daga cikin ƴan gidan su ne "mamar su ko ƙannen ta. Amma sai taga modu ne saurayin da unguwar su ɗaya ɗan maƙotan su ne , cikin sauri ta dawo da baya tare da rike hannayen sa biyu tana haki ,fuskar ta ɗauke da matsanancin tashin hankali take tambayar sa ina mamar ta ina kannen ta ? Amma maimakon ya bata amsa sai taga yana jaan ta da gudu su koma hanyar da ta bullo , da karfi ta fisge hannun ta tare da yi ma sa tsawa tana sake maimaita tambayar ta "Modu nda mamanyi nda kiramiyanyi " ? Yakaka  yanzu ba lokacin tambaya bane domin rayukan mu suna cikin haɗari , ban san inda suke ba , ki zo mu gudu yagana, kashe mutane ƴan tawayen *BOKO HARAM*  suke sun yanka babanmu ,da yaa bakura sun tafi da Fannah da yaakori "(kannen sa) " maman mu ban san inda take ba ita da sauran kannen  mu ,sun ƙona gidan mu da gidan ku da .... Tunda ya fara nisa cikin bayanin sa ta daina fahimtar me yake cewa , zuciyar ta ta tafi ga tunanin me yake faruwa da su ne ?, ta yaya zata rasa kowa da kome nata a yini ɗaya ? Baban ta ya mutu , bata san inda mahaifiyar ta da kannen ta suke ba a mace suke ko a raye ? Ina zata je ? Bata da kowa bata san kowa ba bata taba zuwa ko'ina ba babu inda ta sani bayan ƙauyen su , a hankali ta juya tana nufar cikin garin su hanyar unguwar su cikin ran ta tana aiyanawa gwara ita ma a kashe ta gwara ta mutu . Bata da karfin jiki da na zuciyar tunkarar wannan sabuwar rayuwar da take tunkaro ta wacce bata hango kome a cikin ta ba sai tarin tashin hankali wuya da wahala ,maraici da rashin madafa . Da karfi modu yake kwala mata kira yana so ta dawo su tafi domin shi yaga irin bala'in da bata gani ba da yake cikin garin wanda mutuwa ce murarar ta , mutuwar ma ta walakanci wanda aka harbe da bindiga ya mutu shi ya ji daɗi akan waɗan da aka kwantar aka yi wa yankan rago da waɗan da aka sanya wa wuta suka kone kurmus ,da waɗan da aka jefawa bom yayi kaca-kaca da su . Dan haka ya kasa bin ta ya taro ta "duk da cewa akwai boyayyar soyayyar Yakaka cikin ransa wanda bai kai ga bayyana ta ba" amma baya jin matakin son da yake yi mata ya kai wanda yake yiwa ransa da rayuwar sa baya jin zai iya salwantar da ran sa domin taya ta neman iyayen ta, dan haka ya sake juyawa da gudun gaske yayi gaba ba tare da ya sake waiwayar ta ba , Cikin rashin sanin inda take sanya kafafun take tafiya kunnuwan ta sun toshe daga jin hayaniyar da ta cika duniya, tunanin ta ya bar gangar jikin ta ta yadda har bata jin turewa da bangajewar da mutane suke mata , wanda yawancin su daga unguwannin da suke ƙasa da tasu unguwar  suke fitowa wanda a halin yanzu ƴan tawayen  suke far musu ,.baza ta ce ta yaya aka yi ba kawai taga kanta ne a gaban rugujajjen ƙonannen gidan nasu da har yanzu ta wasu wuraren wutar bata gama mutuwa ba domin tana iya hango hayakin da ya ke turnuke da gidan . Da gudu ta taka ta shiga gidan tana kwalla kiran "mama "yaana "falmata " shiru taji babu motsin kowa , cikin tashin hankali take kallon tsakar gidan nasu da yake a hargitse kamar sansanin yaƙi , kome baya muhallin sa duk da daman su basu da kome a cikin gidan nasu sai tsumokarai da ƴan tsofaffin kayan aikin su na gida wanda su ma a halin yanzu duk a ƙone suke idan ka dauke randar su da take binne cikin ƙasa da gudu ta nufi ɗakin su duk da hayakin da take hangowa cikin ɗakin ta saman sa wanda rufin zanar ya riga ya cinye ,ya zama saman a buɗe yake wayam, hakan bai hana ta cusa kanta cikin ɗakin ba babu  kome cikin ɗaƙin sai burbuɗin tokar wutar da ta gama cinyewa , bakikkirin hayaƙin ma daga kan guntun kayan su ne da ya gama ƙonewa ba jimawa yake tashi . Durƙushewa tayi ta saki wani irin kuka da yake fita daga karƙashin zuciyar ta ,kukan maraicin da ya same ta a rana daya , kukan rasa komen ta da tayi , kukan sabuwar Rayuwar da take fuskanta  . Ta ɗauki tsawon lokaci tana kukan nan har zuwa lokacin da ta fahimci hayaniyar da ta cika garin nasu ta fara raguwa sai tsilla tsilla take jiyo ihu da wucewar mutane a guje , har zuwa lokacin da ta tabbatar dare yayi , ganin duhun da ya mamaye sararin samaniya , da sauri ta miƙe tunowa da tayi bata yi sallar azahar, la'asar, da magarib ba ta kuma tabbatar lokacin isha'i ya yi tana son yin addu'a ta sani bata da kowa bata da kome a yanzu sai Allah dan haka gun shi zata kai kukan ta . Tana fitowa tsakar gidan ta rasa abun da zata yi alwala da shi ,( sakamakon duhun da ya mamaye tsakar gidan, ) da taimakon hasken walƙiyar da take ta haske sararin samaniya, ta hango wani bakin kwanon da duk wuta ta kone sa wanda  ada shine kwanon da suke ji da shi duk gidan kuma shine kwanon cin abincin baban su . Da gudu ta karasa ta ɗauki kwanon ta rungume tare da fashewa da kukan tuno mahaifin ta da gawar sa take can a cikin gona bai samu ko darajar suturtawa a kai sa makwancin sa ba . Bayan ta share hawayen ta takarasa tare da buɗe randar su wacce ita ƙadai ce ba'a tarwatsa ba a gidan su ,"dalilin tana binne ne cikin ƙasa" ta sunkuya tare da buɗe randar , hawayen idanun ta da suka ƙi tsayawa suna ɗiga cikin randar , ta yi goho tare da sa kwanon cikin randar da nufin ɗibo ruwan ciki amma sai taji hannun ta ya tokare bai karasa ƙasan ba sannan kwanon ya bigi wani abu a cikin randa a firgice ! Ta mike jikin ta yana rawa tafara jaa da baya ,tana tunanin menene a cikin randar ? Ji da tayi kamar wata karamar dushashiyar murya tayi magana Daga cikin randar da ya sanya ta sake shiga cikin fargaba !, kuma kamar wacce aka zabura ! Sai ta nufi randa da gudu gami da durƙusawa ta leƙa cikin randar zuciyar ta cike da zumuɗin Allah ya sa tunanin ta ya zama gaskiya . Ai kuwa da sauri ta sa hannu gami da taya ƴar uwar ta ta fitowa daga cikin randar da tayi maboya a ciki wacce bakin ta ya riga ya guntule ya farfashe daga sama ,  tana gama taya ta fitowa ta rungume ta cikin kuka yakaka take tambayar Falmata ina mamar su ? ina sauran ƙannen su ? Cikin kuka da dushewar muryar da bata fita sosai tsabar kuka take cewa lokacin da muka fara jin harbi sosai sai mama ta ɗauki  bulama da yaana, ni kuma ta saka ni cikin randa "saboda tasan bazan iya gudu da sauri ba dan bana GANI " ta ce min zata kai su yaana gona ta boye su ta dawo nima ta ɗauke ni , shine har yanzu bata dawo ba, Yakaka ina baban mu ? Ki kaini gurin sa ya nemo mana mama da su yaana ,,, ina jin tsoro dazu naji mutane har gida suna neman mu inajin ihu a gidan su modu da gidan su yanziye naji suna ihu da cewa wuta wuta , ana ta kuka da salati ina ji ana harbin mutane , meye yake faruwa yau a garin mu ? Jin shiru ya sa falmata ta fara lalube har ta kama hannun yakaka wacce tun da  falmata ta fara bayanin take kuka , kukan mutuwar mahaifin su , da batan mahaifiyar su da ƙannen su , kukan tausayin falmata da take MAKAUNIYA , marar gata marar galihu , daman gatan su Allah sai kuma iyayen su to gashi sun rasa su a lokaci ɗaya , ba iyaye kawai suka rasa ba har da dangin su ƴan uwa , makota da abokan arziki , gidan su da garin su baki ɗaya , dan ko ba'a fada musu ba ta san garin su ya tarwatse , hakan yana nufin sun rasa kome nasu . Wani irin kuka me karfi ne ya kwace mata ta sake rugume kanwar ta tsam-tsam tana jin bata da kowa bata da kome sai Allah sai *FALMATA KANWAR TA* , Kukan su ya tsannanta lokacin da yakaka ta gama sanar da falmata  kome game da mutuwar baban su  , kuka suke an rasa me rarrashin wani a tsakanin su , ga wani irin mugun tsoro da zukatan su ke ciki na rashin jin motsin kowa a unguwar su kusan ma garin nasu baki daya , ga baƙin hadarin da ya hado bakikkirin wanda ya kara wa sararin samaniyar garin da dare ya riga yayi duhu sai walkiya da cida ,alamun ruwan sama gaf yake da fara zuba . A hankali yakaka ta ɗago falmata daga jikin ta tana share mata hawayen da suke zubowa daga gurbin idanun ta wanda idan ba an fada maka ba ko kuma ka lura kaga yadda suke tsaye kem alamun basa amfani uwa uba kagan ta tana lalube , baza ka taba cewa bata gani ba domin tar idanun ta biyu suke a buɗe ,ko meye sanadin makantar ta ? Ko haihuwar ta aka yi da shi ? Ɗaga kai tayi ta sake kallon sama tana tunanin ina zasu samu mafaka daga dukan ruwan saman da yake daf da tsugewa , da sauri wata dabara ta faɗo mata cikin dusashiyar muryar  tace falmata muyi sauri muyi sallah  kin ga ruwa za'a fara ke kuma kin san kina rashin lafiya idan ruwan sama ya doke ki "zazzabi da mura"  dan haka idan mun idar da sallah sai ki koma cikin randar ki bani hijabin ki na haɗa da zani na na rufa a bakin randar sai na daura murfin "wani ƙuzajjen farantin kwano ne" na rufe ki a ciki zuwa lokacin da ruwan zai tsaya sai musan in da zamu yi . gƴada kai kawai falmata tayi , cikin sauri-sauri suka yi alwala suka duddungura sallolin su wanda kana gani kasan akwai ƙarancin ilmin addini a tare da su, ko kafin su gama an fara yayyafi da karfi da ya sanya yagana yanke doguwar addu'ar da ta fara ta kama hannun ƙanwar ta tare da kama mata ta koma cikin randar  . ko kafin ta gama toshe mata bakin randar ruwan ya riga ya tsinke, cikin hanzari ta gama rufewa ta tsugunna a bakin randar daga ita sai rigar ta da ɗankwali sai kuma siket ɗin ciki, haka ta takure jikinta ruwan nan yana dukan ta , ta ɗaura kanta akan gwaiwar ta hawaye yana sauka a idon ta tare da zubar ruwan saman da yake sauka a fuskar ta yana wanken hawayen da yake sauka, bakin ta ɗauke da addu'o'i iri-iri da take yin su cikin yaren ta. Ruwan saman sai yayi kamar zai tsaya sai kuma ya sake tsugewa , a hankali sai da tsakar gidan su ya cika taf da ruwa, " kamar yadda ya saba" cikin karamar muyar falmata ta ankarar da yakaka wacce ta yi nisa cikin tunani har bata jin yawan ruwan da ya haura idon kafar ta ,"ruwa ya fara shigowa cikin randar yakaka,' cikin tashin hankali da sauri ta zame dankwalin kan ta ta matsa ruwan jiki ta sa dankwalin ta toshe hudar jikin randar da ruwan ya ke tsiyaya ciki ta ɓulin, Ta sake tsugunnawa gami da takure jikin ta cikin jin matsanancin sanyi da wani ciwon kai da suka dirar mata lokaci daya , hakoranta sai karo da junan su suke tsabar karkarwa, a hankali ruwan ya fara tsagaitawa bayan kwashe kimanin awa daya da kusan rabi ana tsugawa , sai iska me karfi da matsannancin sanyi ne yake busawo tare da sauran feshin ruwan saman . *************    *MARAƊi Niger République* Jihar maraɗi itace cibiyar kasuwanci a kasar Niger wacce Allah ya albarkace ta da masana'antu , masu kudi, da ma'aikata sanan kuma tana daya daga cikin garuruwa na kudancin Niger karkashin manyan garuruwan kasar hausa kuma ta kasance karkasin mulkin katsina shiyasa ma ake mata lakabi da katsinar maradi domin katsina ta mulke ta tun lokacin yakin kasar hausa kuma hasalima yanzu idan za a kira sarautar maraɗi sai ance sarkin katsinar maraɗi. Kenan zamu iya cewa maraɗawa katsinawa , tun asali Maraɗi tayi yake yake sosai a kasar hausa inda taci nasarar wasu garuruwa wasu kuma su ka bata kashi amma dai tarihi ya nuna bamaraɗe jarumi ne kuma baya tsoro wanan shi yasa ta bunƙasa har zuwan turawan mulkin malaka a kasar hausa inda  suka sha gwagwarmaya da turawa a wancan locakin ,a zamani sarkin katsinar maradi tsakanin shekara ta 1892 zuwa 1894 . Bayan jihadin sheik usmanu fodio inda ya yaki sarakunan kasar hausa ya kuma jaddada addinin islama a wanan nahiyar ya kuma canza sarakuna da dama musaman wadanda suka bijirewa kaidodin sa maradi ta shiga cikin jerin kasashe da wanan abu ya ritsa da su Kuma tasamu sarakuna 23 Tun daga kan Sarkin katsinar maradi  Dan kassawa 1817, 1830 Har izuwa kan na yanzu . Wannan kenan Cikin Tafkeken falon wanda yake ɗauke da kayan ado da alatu , irin wanda ake samun su kaɗai gidan sarakai ,cikin masarautu irin namu na gargajiya , Mutane biyu ne cikin falon Mutumin da kallo daya za'a yi masa a hango girman cikar kamalar sa ,kasaitar sa da mulkin da ke gare shi yana zaune kan ɗunɗumemiyar kujerar da take ware daga tsakiyar falon tana fuskantar duk me shigowa cikin falon . Gefe da gefen kujerar ƴan kananun teɓurin gilas ne dayan teburin saman sa ɗauke yake da ƴaƴan itatuwa nunannu lafiyayyu tun daga kan inabi,ruman ,zaitun,tuffa,tanjari, da sauran manyan ƴaƴan itatuwa masu daraja , ɗayan teburin kuwa ɗauke yake da wata kyakkyawar butar  shayi da take kan wani babban farantin da suka zo tare ruwan zaiba tare da kananun kofunan ta da chokulan da daga  gani du tare suka zo , Daga kasa kuma tsakanin kewayen manya-manyan kujerun da suka yiwa tafkeken falon ado , wani dogon saurayi ne wanda bayan sa kawai za'a kalla a gane tsawo da cikar halittar sa ta ɗa namiji kansa a sunkuye ,kafafun sa a tanƙwashe yayi zaman raƙumma gaban wannan mutumin yana sauraran duk wasu kalamomi da suke fitowa daga bakin sa ɗaya bayan ɗaya , da yake cewa , YOUSSOUFA na samu sakon bukatar da Ka zo da shi ,sai dai ina bukatar jin ƙarin bayani daga gare ka ,? Cikin kwantar da murya wanda aka kira da youssoufa ya ce ranka ya dade kamar yadda na fada wa jakadiya , wani aiki ne ya taso daga gwamnatin kasar nan wanda ta zabi sojoji kimanin dubu ɗaya da ɗari biyar,  ta kuma wakiltani a matsayin shugaban su da zan jagorance su zuwa kai tallafin gaggawa ga yankin makociyar mu kasar Nigeria akan ƴan tawayen nan na boko haram da suka addabi yankin arewacin kasar wadda idan muka yi wasarere mu ma annobar tana iya shafar kasar mu nan Niger saboda boda da makoftakar da muke  da juna ta kurkusa ,ya ɗan tsagaita gami da ɗaga kai ya kai kallon sa ga fuskar mutumin da ya zuba masa ido yake saurarar sa da dukkan hankalin sa. Sake sunkui da kai yayi gami da cigaba da cewa shine nake neman alfarma akan a ɗaga biki  zuwa lokacin da zan dawo wanda nake tunanin ba zai gaza nan da shekara ɗaya ba , do Allah ayi mini alfarma mai Martaba ,"ya karasa furta hakan cikin marairaicewa da kwantar da murya " ? Ɗan gyaran murya yayi kafin yace ,wagga lamari naka da ban mamaki ike kai youssoufa anya aikin taimakon ƙasa zai wucce raya sunnah ?   ɗan jim yayi ɗaga bisani yace tashi kaje du shawarar da muka yanke tana iso maka ta hannun jakadiya , Ras-ras yaji zuciyar sa ta tsinke tun da Mai Martaba yace sai yayi shawara yasan bai gamsu ba bai amince da alfarmar da ya nema ba hakan yana nufin bazai amince masa ya tai zuwa nigeria  wanda kuma hakan yake dai-dai da rasa aikin sa da tun da yayi wayo a duniya ya san soja ya kasance  bashi da wani burin  da ya wuce ya zama SOJA , duk da kasancewar sa ɗan sarki kuma BIYAMARADI , haka ya dunga kawar da duk wasu kalubalen da zasu shiga tsakanin sa da cikar burin sa ya shaa gwagwarmayar da ta kawo sa kan matsayin da yake na yanzu me amsa cikakken sunan COLÓNEL YOUSSOUF ABDOUL AZIZOU BASKORE !!!!!!!.... [6/24, 9:49 AM] +234 701 013 7848: Fikrah writers association *MAFARI.......* ( _HARGITSIN RAYUWA_ )              *Umm'muaz* 2 Cikin sanyin jiki tare da rashin kuzari yake takawa yana wuce zauruka da sashi sashi kamar yadda aka San tsarin ginin masarauta yake. Jerun gwanon bayin sa su rai biyar suna biye da shi tun daga ƙofar fada inda ya amsa kiran Mai martaba , tafe yake cikin kasaitar da ta amshi tsarin zubin sa na ingarman namiji dogo da ya kere dukkanin mutanen da suke tare da shi tsawo a lokacin. fuskarnan tasa a murtuke kitib ya fito a SOJAN sa sak kuma BIYAMARADI, baya ko amsa gaisuwar bayin da suke ta faman zubewa a ƙasa suna kai gaisuwar su tare da kirarin da suka saba yi masa. Biyamaradi dan sarki mai jiran kujerar mulkin kassar mu albarka, kayi gadon mai martaba. Biyamaradi jarumin jarumai, biyamaradi namijin, ayi yau ayi gobe sai gaskiya jibi rago ya kassa. Dan sarki mai makaman yaki, Dan sarki mai ado. Biyamaradi kai zaki ne mai watsar da taron maza Dan sarki mai tarin illimi to kayi ga arabi ga boko wallahi ka kure tunanin Masu tunani. Allah.ya kare ka gwani na hattara biyamaradi. hattara biyamaradi. Hattara biyamaradi HATTARA BIYAMARADI  Sai dai ga Biyamaradi yousoufa a yanzu sam basa burge shi basa sanya shi nishaɗi , babu abun da yake sanya shi nishaɗi a yanzu irin karar kafafuwan sojojin da suke jaan tunga su ƙame masa idan sun hango shi , babu muryoyin da suke burge shi irin na amsawar sojojin da ke karkashin ikon sa idan ya basu umarni , Dai-dai ya zo shiga sashin sa da yake bangare guda ko kuwa ɗaula guda a cikin gidan nasu ya ga wani hadimin sa ,wanda yana karasowa wajen ya zube ƙasa yana ƙirari tare da kai gaisuwar sa , bayin da suke tsaye a bayan sa su suka amsa da " Biyamaradi ya amsa gaisuwar ka meke tahe da kai ? " yana daga durkushe yake isar da sakon dalilin tsayuwar sa anan "jakadiya" ce tace ya zo ya jira shigowar yarima ya koma ya sanar da ita . yana jin abin da bawan nan ya faɗi ya sanya kansa gaba gaɗi ya shiga gidan sa tare da yi wa bayin alama na kadda su biyo bayan sa , ( domin shi ya tsani taron bayun nan da suke zuwa du su zagaye shi su hana shi sakat ko wanne motsi yayi idanun su na kai suna yi masa surutun banza"kirari" a cewar sa) babu wanda ya motsa daga inda yake cikin bayun nan domin idan da sabo yaci ace sun saba da tsarin halayyar BIYAMARADI" Yousoufa shine ɗa na biyar a wurin mai martaba ɗa na huɗu a wurin mahaifiyar sa , kuma ɗa namiji na farko a gidan baki ɗaya , mahaifiyar sa ɗiya ce ga sarkin birnin gaoure, ita ce ƴa ta biyu cikin jerin ƴaƴan mai martaba Lamiɗo " Bafullatana ce gaba da baya kamar yadda kowa yasan birnin gaoure garin hullanin usul ne , Mahaifiyar yousoufa da mai martaba(sarkin maraɗi ) auren so da kauna suka yi , tun lokacin mai martaba bai kai ga hawa kujerar mulkin birnin maraɗi ba suka haɗu a wurin bikin yaye ɗalibai ƴan makarantar gaba da primary ta makarantar "École Bedir" da ke birnin Niamey a wancen zamanin da sai ƴaƴan wane-da-wane ke yin makarantar ,kanwar mai martaba " Zainab tana cikin ɗaliban da aka yaye a wannan shekarar ta alif dubu ɗaya da ɗari tara da saba'in da tara 1979, "wanda shi mai martaba Abdoul azizou ya wakilci mahaifin su wajen taron a lokacin shi ɗalibi ne a jami'ar Abdoul Moumouni Diof da ke nan cikin birnin Niamey" Anan yaga safiyya , tana ɗaƴa daga cikin ƴan matan da aka zaɓa domin su gudanar da ƴar kwarya-kwaryar wasan koikoyo da akan yi lokacin bikin yaye ɗalibai , kallo ɗaya yayi wa ƴar fulanin yaji ta kwanta masa ya kuma ji cewar ya samu matar aure , Bai yi ƙasa a gwaiwa ba ya sanarwa zainab tare da gwada mata yarinyar daga nesa lokacin da aka kammala taron ana shirin watsewa nan take kuwa zainab ta shaida ta domin ta san safiyyah farin sani hasalima tamkar kanwar ta take domin koh lokacin da aka kawo safiyyah ajin farko a makarantar ita kuma tana aji na uku a lokacin ɗakin kwanan su guda su biyu ne rak a ɗakin kasancewar haka tsarin ɗakunan kwanan ɗalibai na makarantar yake, mutane bibbiyu ne a kowanne ɗaki , sun shekara guda tare cikin aminci har zuwa lokacin da ita zainab ta shiga ajin manyan ƴan secondry "aji huɗu" a lokacin ne aka sauya mata ɗaki ta koma saman bene a hawa na farko , Hakan ne yasa koh da yayan ta ya nuna ra'ayin sa akan safiyyah taji dadi sosai kuma ta wuce masa gaba ta gabatar da shi a wurin safiyyah duk da cewa dai ita a lokacin ne ma take aji na huɗu , Amma tayi na'am tare da maraba da bamarɗe Abdoul azezu . Haka dai tafiya sannu-sannu suna tare cikin aminci da so da ƙaunar junan su har zuwa lokacin da safiyyah ta kammala karatun gaba da primary a shekarar mai martaba sarki Youssoufa Baskore mahaifin "Abdoul azizou ƴa tura da takardar neman aure da kayan nagani ina so ga masarautar sarki lamiɗo na barnin gaoure inda shima bai yi kasa a gwaiwa ba ya amsa cikin tsantsar farin ciki da lamarin "domin a garesu hakan babbar nasara ce kasantuwar kowa ya san sarautar maraɗi ita ce ta biyu a karfin mulki kaf kasar niger " Aka tsaida ranar auren su sha biyar ga watan satumber na shekarar alif dubu ɗaya da ɗari tara da tamanin da ɗaya "15-sept-19981, rana ta zo aka sha biki amarya ta tare a gidan mijin ta sasahi guda a cikin gidan sarautar maraɗi . Kwance tashi rayuwar su ta fara miƙawa cikin aminci fahimtar juna da tsantsar ƙaunar junan su , Allah ya Albarkace su da haihuwar ɗiya mace shekara ɗaya da auren su wacce ta ci sunan marigayiya mahaifiyar su Abdoul-azizou wacce ta jima da rasuwa tun su na yara ,"Halimatu'sa'adiyyah" ana kiran ta "Ammi" Tsakani shekara biyu cif da safiyyah ta sake haihuwar ɗiya mace aka sanya mata sunan mahaifiyar safiyyah "Suwaiba" ana kiran ta "dada " Bayan watanni tara da haihuwar "dada " safiyyah ta sake samun ciki ta haifo "zainab" wacce ta ci sunan kanwar Abdoul-azizou sai ake kiran ta "ubbo" Tun daga nan fa sai mai martaba sarki Youssoufa ya ce Abdoul-azizou sai ya sake aure koh ya samu magaji tun da ga alama matar sa uwar ƴan mata ce , babu yadda Abdoul-azizou bai yi ba akan ya fahimtar da mai martaba haihuwa kyautar Allah ce babu ɗiya mace koh ɗa namiji dukkaninnsu ɗaya ne har kullum masu albarka ake nema . Sai dai fir mai martaba yaki saurarar sa domin a gefe guda "hajiya uwa " da takasance matar sarki ta biyu "wacce take matsayin babbar matar sarki tun bayan rasuwar mahaifiyar su Abdoul-azizou " a lokacin ta samu wuri sai daɗa hura wutar kiyayyar ɗiyoyi matan da ake haihuwa a gidan abdoul-azezu take " a cewar ta sarauta ta kama hanyar barin hannun Baskore tunda ga alamu Sarautar tana dakatawa ne akan Abdoul-azizou da yake a matsayin yarima a lokacin , Ba tare da neman shawarar Abdoul-azizou ba mai martaba ya nema masa Auren ƴar abokin sa kuma yayan matar sa "Hajiya uwa "Babban Limamin Maraɗi "Malam muhammadou" wacce ake kira "Saratu " . Tare da sa hannun hajiya uwa wacce tayi ɗare-ɗare akan harkar bikin nan tayi uwa tayi makarɓiya , ranta ƙwal ! tana ƙitsimawa "idan sarauta ta kuskure masu ta wani wuri kasancewar ita bata taɓa haihuwa ba toh tabbas ga sarautar nan dawo masu ta wani hannu " tana da tabbacin daga saratu ta zo ta haifi ɗa namji shikenan sarauta ta zamto tasu. Saratu ita ce ɗiya ta shiddah cikin jerin ƴaƴan Liman muhamdou , mahaifiyar ta tun tana ƴar shekaru biyu suka rabu da mahaifin ta "mahaifiyar ta ƴar Nigeria ce a can wani gari da ake kira zuru a ƙasar kebbi Nigeria , Saratu ta taso tsakanƙanin matan uba , babu irin izaya da wahalar da ba'a gana mata ba , shi ya sa ta tashi a kangare sannan me mummunar zuciyar da take cike da ƙudirin ɗaukar fansa, Lokacin da ta shekara goma sha biyar ta kasance fanɗararriyar yarinya ce ta kin ƙarawa wacce tun da ta fara girma ta buwayi matan mahaifin nata da fitsara da raini uwa uba saratu ta kasance me matukar fasahar iya shirya zancen ƙarya da tuggu domin ta tada husuma a tsakanin matan mahaifin ta duk a cikin mummunan ƙudirin ta na ɗaukar fansa . A take -take zata haɗa zantukan ƙarya ta ɗora mutum kome girman sa akai kuma ya hau ya zauna daram , saboda tsabar yadda ta iya shirin ƙarya , wasa-wasa sai da ta maida gidan mahaifin ta sansanin yaki a wurin matan gidan , kullum cikin faɗa ake kamar garken karnuka , ita kuwa ta koma gefe tana wake-waken ta ,bayan idanun su ta shiga ɗaki ta ci dariya son ran ta ta fito tsakar gida tana karya wuya tare da bai wa wacce ta zuga hakuri .(Saratu kenan , ƴar malam wacce taƙi halin malam ) A tsakanin matan mahaifinta su uku babu wacce ta kai ga fahimtar hallayar saratu na karya da munafurci "sakamakon rashin haɗin kan su tare da zazzafan kishin su tun asali " sai shi mahaifin nata ne da kan sa ya fahimci "saratu ita ce matsalar gidan sa " yana tunanin yadda zai iyi ya samu ya kawar da ita daga gidan sa "( ya aurar da ita ) . Sai ga sakon kira daga mai martaba "Liman bai yi ƙasa a gwaiwa ba "ya amsa kiran da ya sanya shi kwanan farin ciki bibbiyu na farko dai farin cikin zai zama surikin yariman maraɗi a yanzu , kuma surikin sarkin maraɗi a gobe idan da rai , uwa uba zai rabu da annobar da ta ke sanya shi fargabar shigar sa gidan sa a kullum, Dan haka cikin rawar jiki da murnar sa da ta kasa boyuwa ya amsawa mai martaba sarki youssoufa , ya bawa yarima Abdoul azizou auren Saratu koh gobe ake so a ɗaura ya shirya , cikin farin ciki da karamci da aka nuna masa Sarki youssoufa ya tsayar da ranar ɗaurin auren Abdoul azizou da saratu ranar ishirin da biyar ga watan sha biyu shekara ta alif dubu daya da ɗari tara da tamanin da biyar 25-Dec-1985 . A daren ranar ya aika aka kira masa yarima abdoul azizou , in da ya sanar da shi hukuncin da ya yanke tare da bashi umarnin ya shirya gobe da Maraice ya je su ga juna shi da saratu ɗiyar liman domin kwanaki ishirin da ɗaya kachal suka rage a ɗaura musu aure , Ba tare da yarima Abdoul azizou yana fahimtar sauran kalaman bakin mai martaba ba ya amsa masa gami da yi masa godiya da sallama ya fito daga turakar mai martaban zuciyar sa cike da zogi da raɗaɗin bacin ran tashin hankalin da yake iya hango samuwar sa tsakanin sa da abar son sa "safiyyah " Tabbas shi yasan yadda safiyyah take tsananin kaunar sa da kishin sa , yasan duk lokacin da ya je mata da labarin auren da aka riga aka nema masa ya kuma zama dole a gareshi ya amsa hannu bibbiyu , kasantuwar bai taɓa musantawa mahaifin sa ba akan duk wani hukunci da ya yanke a rayuwar sa domin shi mutum ne me ilmin addini sosai , yayi karatu sosai arabi da boko ya san irin haƙoƙin da iyaye suke da shi akan ƴa ƴan su hakan ya sa ya kasance ɗa mai tsananin biyayyah ga iyayen sa . Dan haka a yanzu ma yayi aniyar karban auren da za'a yi masa da hannun aminci duk da cewa shi ba son auren yake ba asalima bai taba kawowa ransa sake yin aure nan kurkusa ba kamar yadda tun da yake bai taɓa son wata ɗiya mace irin son da yake yi wa safiyar sa ba kuma baya jin zai sake son wata ƴa mace irin son da yake yi mata " ya ajiye auren da za'a yi masa a karo na biyu a mizanin kaddara " Sai dai babbar matsalar sa a yanzu tunanin hanyar da zai bi ya tunkari saffiyah da batun karin auren sa ,"a daren yau din domin baya son ma lamarin ya kwana ba tare da ya fitar mata da hakkin ta ya sanar mata ba a matsayin ta na matar sa da suke zaman aminci , kaunar juna da fahimtar juna " sai dai ya san mata idan aka zo batun kishiya ba dama ne ' Haka dai ya shiga gidan nasa baya sun natsa ya fuskance ta da maganar auren , sai dai ga mamakin sa ,' bata tayar da hankalin ta irin yadda yake zato ba hakan kuwa yana da nasaba da zancen ya riga shi isowa zuwa kunnuwan ta " Abun nufi ta ji zance a cikin gida " abun ka da gidan sarauta da kuma yadda ya kasance hajiya uwa tana ta yamiɗiɗi da zance tana yada magana tare da fiffikar ta ta zata shigo gidan " da farko bata fahimci zancen ba sai da ta tambayi jakadiyar sarki ta wancen zamanin ita ce ta warware mata zare da abawa ta kuma kwantar mata da hankali tare da bata shawarwarin alkhairi da za su taimaka mata. Amma duk da haka bayan dawowar ta sashin ta yini tayi tana kuka tare da tunanin ƙalubalen da yake fuskanto ta "abu ɗaya ne ya rage mata jin zafi ji da tayi matar da za'a aurawa mijin nata ba ƴar wani babban sarki bace ko kuwa wani hamshaƙin attajirin da kasa ta san da shi ba " Ƴar Limamin Maraɗi ce hakan sosai ya rage mata zafi kasancewar safiyyah irin ƴaƴan sarautan nan ce masu ji da kan su da nuna isa sosai jinin sarauta na ƙasaita , da iko suke yawo a jikin ta ta yadda take ganin duk wani wanda ba ɗan sarautar da ya kai ya kawo ba a matsayin kasasshe a wurin ta, safiyyah tana son sarauta tana alfahari da sarauta tana kuma ƙaunar masu sarauta , bata daukar mutanen da basu da sarauta da wani muhimmanci a rayuwar ta . Dan haka koh lokacin da ranar da aka yanke na ɗaurin auren Abdoul-azizou da saratu ya zo , aka kuma ɗaura auren cikin kwanciyar hankali tare da bakukuwa kamar yadda yake a al'adar su , sam safiyyah bata bayyana matsanancin tashin hankalin ta ba duk kuwa da cewar abun yana nuƙurkusar ta a karkashin rai !Saboda yadda take kaunar mijin ta sai ga shi a yanzu ya zama nasu ita da wacce take ganin bata kai matsayin ta haɗa kafaɗa da ita akan abun da take so ba . Hakan ya sa bayan tarewar Saratu "a sashin ta da aka gina mata daura da sashin Safiyyah ta hannun hagu "Sam safiyyar bata shiga harkar Saratu "A ganin ta saratu bata isa tayi gogayya da ita ba " "iyakaci idan sun haɗu a cikin gida 'idan sun je gaishe da hajiya uwa da sauran matan mai martaba biyu "Hajiya mai karamin ɗaki da umma Amarya " " su gaisa da juna sama-sama, sosai ita saratu take jin zafin yadda safiyyah ta tattara ta tare da shirgin ta ta watsar a gefe take nuna kamar bata san ma da zaman ta a cikin gidan ba , " Hakan yana kona ran ta , domin ita ta shigo gidan ne da nufin ta dunga bi ta ƙasa-ƙasa irin yadda ta saba ( a gidan mahaifin ta) tana tunzura safiyyah tana tada bala'i a tsakanin ta da Abdoul-azizu har dai tayi nasarar dusashe karfin soyayyar da ta lura Abdoul-azizu na yi wa safiyyah ,ta yadda ya kasance idan suna tare koyaushe bakin sa cikin ambaton Alkhairin safiyyah da kyawawan halayenta tare da yabawa safiyyar yake ," Sai dai bata samu damar hakan ba domin duk wata kafar da zata bata damar aiwatar da mummunan nufin ta safiyyah ta toshe "ta hana ta fuska " A cikin hakan ta fara laulayin ciki bayan watanni biyu da auren su "wanda kuma kusan tare suka ɗau cikin da safiyyah " domin ita ma tana ɗauke da ɗan tayin cikin ta na wata ɗaya " . Nan fa Saratu ta samu abun yin lanɓo ,kitifiri da feleƙe , ita a dole ga mai juna biyu " cikin yana wata uku su ka fasa Sanarwar ai Malamar jinya a asibitin da take zuwa awo a wancen zamanin ta tabbatar mata da cewa "Ɗa" namiji zata haifa ' Sanarwar ta fito ne ta bakin "Ɗan Zagii" a karkashin jagorancin "Hajiya uwa "wacce ita ma saratu ce ta yi mata Albishir tare da tabbatar mata da abun da malamar jinyan ta faɗi gaskiya ne "cikin rashin sanin Hajiya uwa cewa zancen ƙarya ce tsagoronta wacce ita Saratu ita ta haɗa zancen ta sakamakon jin wata matar babban likita da suka haɗu da ita wurin awu tana bada labarin injin awun da yake bayyana jinsin jariri tun yana cikin mahaifiyar sa " ( Asalima a wancen zamanin injin yin awun da ke gano jinsin halitar da yake ciki bai riga ya bazu a kasashen africa ba ) Nan take zance ya kewaya fada har ya isa kunne mai martaba ta bakin jakadiya " sosai mai martaba yayi farin ciki tare da bada goron Albishir me yawan gaske" A bangaren Yarima Abdoul azizu shima yayi matuƙar farin ciki da wannan albishir har ma ya gaza boyewa ya bayyana farin cikin sa a sarari gaban idanun safiyyah tare da nuna ɗokin sa akan samun ɗa namiji da zai yi nan ba da daɗewa ba "wanda hakan ya tashi hankalin safiyyah a karon farko tun bayan auren sa da saratu "Amma sai ta share ta taya shi murna a sarari "duk da cewa cikin ran ta taso a ce ita ta haifo magajin maraɗi saboda kaunar ta da sarauta ", Sai dai kasancewar ta ƴar sarauta ta kasance me iya boye hakiƙanin cikin ta, ya sa ba wanda ya fahimci halin da zuciyar ta ke ciki , hatta Saratu wacce take yin duk wani kilbibin ta da biyu 'dan ta turawa safiyyah haushi " ta gaza ganin bacin ran safiyyar . cikin watannin girman cikin kafin zuwan ranar haihuwar sa kaf an gama tanadin kayan jarirai na ɗa namiji wanda wasu ma mai martaba da kan sa ya sayo su a tafiyar sa Umrah , tarairaya da kulawa kuwa babu irin wacce Saratu bata samu tun daga kan surukan ta hajiya uwa da sauran matan mai martaba "da kusan suke karkashin ikon hajiya uwa "har zuwa kan shi kan sa mai martaba, da uban gayya yarima Abdoul-azizu wanda shima zuwa lokacin zuciyar sa sosai ta rinjaya ga son haihuwar ɗa namiji sakamakon "janye hankalin sa ta siyasa da hajiya uwa da saratu suke yi " Wanda har hakan ya soma taɓa amintaccen zaman su na fahimtar juna da su ke shi da safiyyah. Ranar biyu ga watan ɗaya na shekarar alif dubu ɗaya da dari tara da tamanin da bakwai ,2-jan-1987 Saratu ta wuni tana naƙuda taci wahala sosai , kafin zuwa maraice ta haifo Santaleliyar ɗiyar ta mai kama da ita sak " An ɗauki tsawon mintoci uku a ɗakin haihuwar da yake cikin baban asibitin maraɗi bayan bayyanuwar kukan jaririyar da likitocin da suka karbi haihuwar suka tabbatar wa hajiya uwa wacce take tsaye a dai-dai kan saratu tana ta faman jera mata sannu , cewar Saratu ɗiya mace ta haifa har ma suka ɗago Santaleliyar jaririyar da ba'a ce yanzu aka haife ta ba saboda girman ta suka nuna wa hajiya uwa da saratu, shiru ne ya ratsa tsakani kafin Muryar hajiya uwa ta bayyana Cikin cewa". Saratu kika ce Malamin jinya ya tabbatar miki Ɗa namiji ne a cikin ki ? watau ashe zancen ba haka bane ? ashe dai zance Altine "yayar saratun da suke uba ɗaya " zancen ta gaskiya ne da take cewa ke Saratu ba ƙaramar maƙaryaciyar yarinya bace " , Amma ban yi zaton karyar taki da yauɗarar ki ta kai har haka ba , da har domin rashin hankali zaki yi irin wannan ƙasurgumar karyar da yaudarar a gidan sarauta, toh Maza sai ki tanadi ruwan wanke kan ki a idanun mai martaba da shi kan sa mijin naki , ki kuma tabbatar kin riga kin gama zubda ƙimar ki a idanun mutanen gidan nan ciki kuwa har da bayun da suke karkashin ki , haba saratu me ake da wannan irin karyar taki " Saratu dai babu bakin magana sai sharar ƙwalla take "wanda hakan ya jaa hankalin malaman jinyar da suke gyara ta har ta kai su ga tambayar dalilin kukan ta "hajiya uwa" ta faɗe musu biri har wutsiya akan yaudarar da saratu tayi mata da kunyar da ta jefe ta " Malaman jinyar su da kan su sun ga rashin kyautawa, tare da mamaki irin karyar saratu sai dai sun bada tabbacin akwai irin na'urar a kasashen da suka cigaba ,"sai dai koh na'urar ma ba koyaushe take bada bayanin gaskiya ba"( Sanin gaibu sai Allah ) jin hakan ya sa "Hajiya uwa jin wani farin ciki ko ba kome sun samu hanyar da zasu fidda , kan su " Haka aka gama gyara ta tare da jariryar aka tura su ɗakin da zasu zauna "a lokacin ba'a sallamar mace daga haihuwar ta har sai ta zauna a asibiti kwanaki biyu zuwa uku domin tabbatar da karfin jikin ta " Bayan isar su ɗakin hutun kafin jama'ah su zo "Hajiya uwa ta sanar da Saratu shawarar da ta gama yankewa domin samun rufin asirin su ,nan take yanke "ba tare da jaa ba" Saratu ta amince . Da zuwan yarima Abdoul-azizu "hajiya uwa ta sanar masa da ɗiya mace aka haifa ba ɗa namiji ba ta kuma ɗora da bayanin da malaman jinyan nan suka yi musu na cewa ana iya samun kuskuren inji wurin bayyanuwar jinsin abun da ke cikin mahaifiyar sa " Ƙwarai yarima abdoul azizu yayi kokari wurin nuna rashin damuwar sa akan kuskuren na'urar da ya riga ya yadda akan cewa an samu " Amma cikin ran sa sam sam lamarin bai mar daɗi ba sun riga sun ƙwaɗaitar dashi son haihuwar ɗa namijin . Bayan isar labarin haihuwar saratu "Fada " tare da sabon sauyin da aka samu daga haihuwar ɗa namiji da ake sa ran haihuwar sa zuwa samun labarin haihuwar ɗiya mace , Fada ta shiga Alhini da har hakan ya gaza boyuwa akan fuskar mai martaba , Haka aka yi bikin suna cikin rashin Armashi bayan dawowar su daga asibitin "inda yarinya taci sunan "hajiya uwa Asma'u " Sau ɗaya mai martaba ya sa aka kai masa yarinyar turakar sa "a washegarin dawowar su daga asibiti" in da yayi mata huɗuba tare da bata suna " tun daga ranar bai sake waiwayar su ba. Ga bangaren safiyyah har ila yau dai bata bayyana wani alama ba ta bangaren ta ,na farin ciki koh saɓanin sa akan sauyin jinsin abun da Saratu ta samu . Ita ma tana fama da nata cikin , da yayi wani irin mugun girma fiye da sauran cikin ta guda uku na baya , hakan ya sa da zainab ta zo bikin sunan ɗiyar Saratu "ta nemi da ta ɗauki Zainab "ubbo"(takwarar ta ) Kasancewar tun da aka mata aure a lokacin shekarun auren ta bakwai bata taɓa samun haihuwa ba "sai bari da take ta faman yi " ganin yadda cikin yayi wa safiyyah nawi ga kuma rigamar zainab wacce ba ta kai ga cika shekaru biyu ba a lokacin "sannan gata da jarabar ƙiuya bata yadda da tarin bayu da suke cike da bangaren nasu da ma gidan baki ɗaya "sai jikin uwar ta , ya sa ta nemi tafiya da ita nan take kuwa safiyyah da Abdoul azizu suka bata zainab ɗin ta tafi da ita " Ranar goma ga watan biyu na shekarar alif dubu ɗaya da ɗari tara da tamanin da bakwai 10-feb-1987 ita ce Ranar da ta zamto ranar farin ciki ranar da baza'a manta da ita ba a tarihin masarautar maraɗi ranar da ta shiga jeru ranakun tarihi, Ranar da aka wayi gari gimbiyyah safiyyah tana nakuɗa , zuwa hantsi ta haihu lafiya " farin ciki ne ya wanzu akan fuskar gimbiya safiyyah a lokacin da malaman jinƴar da suka karbi haihuwar ta su ke tabbatar mata da ta samun Ɗan ta namiji 'Ƙato da shi jazir ya ɗauko hasken fatar ta irin ta fulanin usul yayin da tun kallon farko da tayi masa bayan da "malaman jinyan suka gama wanke mata shi tare da shirya shi cikin kayan jarirai" tana yi masa kallo guda ta hango tsantsar kamannin sa da kakan sa"mai martaba sarki youssoufa " kamar an tsaga kara , kakaf cikin ƴaƴan da ake haihuwa a gidan babu wanda yayi kama da Mai martaba irin wannan jaririn "Cikin nutsuwa ta dunga kwararo masa addu'ar kariya kamar yadda take jin matsananciyar kaunar sa tana kwarara cikin zuciyar ta da wani al'amari mai girma irin wada bata taɓa jin sa akan sauran ƴaƴan ta ba"cikin nutsuwa ta ɗaga shi dai-dai fuskar ta gami da sumbatar goshin sa , da kuncin sa dama da hagu, Dai-Dai lokacin da yarima Abdoul azizu ya karaso ɗakin , farin cikin zuciyar sa ya kasa boyuwa daga zuci har zahiri bakin sa ya gaza daina furta kalmomin godiya ga ubangijin sa , ba tare da lura da wurin da suke ba ya haɗa su baki ɗaya ya rungume su , zuciyar sa tana buɗewa tare da sabuwar ƙaunar uwar da ɗan ta , Biki sosai aka dunga yi tare da yanke-yanke ana sadaka domin nuna farin cikin wannan haihuwar , har zuwa ranar da takasance ranar raɗin suna , ɗaruruwan mutane suka hallarci wurin bikin raɗin sunan inda yaro yaci sunan "mai martaba "Youssoufa" A nan wurin kuma mai martaba ya Sa aka yi shela akan bai amince ba a boyewa yaro sunan sa "laƙani " a kira yaro da sunan sa Yarima Youssoufa Abdoul-Azizou Baskore Sunan sa kenan .''' Bayyana irin bacin rai da bakin cikin da hajiya uwa da saratu su ka shiga bai kwatantuwa "domin a ranar da labarin haihuwar ya iso musu kwana suka yi basu yi bacci ba suna jimami da taya junan su bakin ciki " Amma da yake dukkanin su sun ƙware a harkar kissa da kilbibi , sai suka shafe , hajiya uwa tayi ruwa tayi tsaki akan harkar mai jego da jaririn ta , tayi ƙabe ƙabe akan harkar kome , "ta nuna jika dai nasu ne " Haka ita ma saratu take wuni a sashin safiyyah tana taya ta raino "a cewar ta " sosai ta sake a cikin jama'a ana ta hidima da ita "yayin da take nunawa mijin ta da ma ita safiyyar cewa youssoufa ita ma ɗan ta ne " (cikin rashin sanin su saratu da hajiya uwa suna nan ƙudurce da mummunan ƙudirin su da su kadai suka barwa kan su sanin sa , Sai kuma Allah wanda yake masanin kowa da kome ) kwance tashi youssoufa yana girma har zuwa lokacin da ya cika shekaru biyu a lokacin ne babban rashi ya samu birnin maraɗi , in da mai martaba sarkin youssoufa ya amsa kiran mahaliccin sa bayan ƴar gajeruwar jinya , haka aka gudanar da zaman makoki cikin alhinin rashin wannan adalin sarki nasu , bayan an share makoki akayi bikin naɗi inda "Yarima Abdoul azizou ya ɗare kujerar mulki "ya zama sarki " a kuma tsukin kwanakin Saratu ta sake haihuwa inda ta sake samun ɗiyar ta mace "wacce taci sunan mahaifiyar ta Maryam" bayan watanni biyu safiyyah ita ma ta ƙara haihuwar ɗan ta namiji ,"da aka sanya masa sunan lamiɗo " Lokacin da Biyamaradi youssoufa ya cika shekaru biyar da watanni a lokacin ne wani babban rashin ya sake samuwa , Allah ya yiwa zainab kanwar mai martaba rasuwa a wurin haihuwa , ta mutu ta bar ƴar jaririyar ta da ta haifa wacce koh samun damar ganin fuskar ta bata yi ba mai rabawa ta raba " bayan share zaman makoki An samu saɓanin ra'ayi akan wacce zata yi rikon jaririyar zainab da ta ci sunan kakar ta ta wurin uba "siyama " A karshe an tsaida shawarar "safiyyah ita zata yi rikon siyama tare da jaririn ta da ta haifa kwanaki arba'in da suka wuce "Aminu " a dalilin sanin da kowa yayi cewar akwai aminci tare da ƙauna mai karfi a tsakanim marigayiya zainab da kuma safiyyah " domin tun ranar da akayi rasuwar ma jaririyar take karkashin kulawar safiyyah ita take kula da ita ,"take shayar da ita maɗarar da aka tanada domin jarirai sabuwar haihuwa " Dan haka aka miƙa rikon siyama ga safiyyah tare da mayar mata da ƴar ta hannun ta zainab karama "ubbo" wacce a lokacin take da shekaru bakwai tana aji biyu na primary amma sosai ta shaƙu da uwar goyon ta , babar ta ,kuma takwarar ta marigayiya zainab a saboda rikon gaskiya soyayyah da amana da tayi mata " hakan ya sa ta ɗauki son duniya ta ɗora akan wannan jaririyar da take yi wa kallon ƙaramar kanwar ta take kuma son ta fiye da kannen ta da suka fito ciki guda " Cike da ƙauna da tsaftataciyar soƴayyah safiyyah ta karbi riƙon siyama "gefe guda na zuciyar ta kuma ɗauke da wani babban burin da take fatan kasancewar sa , wanda ta riga ta ayyana shi akan jaririyar da aka bata amanar ta " Bayan maryam ita ma saratu ta sake haihuwar ɗiyar ta mace "da ta amsa sunan hauwa"u " , kuma ita ce aka yi goyon su tare da su siyama da aminu " Zuwa lokacin saratu kakaf ta gama bin gidajen bokaye da ƴan bori akan su taimaka mata ta samu haihuwar ɗa namiji "wanda ita ma zata ɗaga tace wannan ɗan ta ne namiji amma shiru ake ji "wai malam ya ci shirwa " akan cikin 'hauwa'u babu irin tsubbace tsubbacen da basu yi ba ita da hajiya uwa wacce har zuwa lokacin bata saduda ba . A gefe ɗaya suna nan suna shirin kaddamar da mummunan aikinsu , kwanci tashi yara suna girma Arzikin iyayen su yana sake bunƙasa ,cigaba da wayewa yana sake yawaita , sauye-sauye suna samuwa , yanayi yana juyawa , *2005* yanayin ya juya ta inda ya mayar da kananun yaran nan wasu matan aure wasu kuma samari " inda ƴaƴan sarki Abdoul azezou Baskore suka cika su Goma sha biyar cif-cif , siyama da ita ma take amsa sunan ɗiyar gidan ta cikace su suka zama su goma sha shiddah cif cif "safiyyah tana da takwas ,Huɗu maza huɗu mata "Saratu tana da bakwai shiddah mata ɗaya namiji ' , An rufe haihuwar da ɗiya mace kamar yadda aka buɗe ta da diya macen ," Biyamaradi yousoufa tun tasowar sa mutum ne miskilin gaske marar son hayaniya "yana da tsananin tausayi ko ma ace rauni akan mata da yara kanana " , baya shiga harkar kowa a gidan babu me ganin fara'ar sa idan aka ɗauke iyayen sa , sai kuma abokin sa , kuma Aminin sa Tafeedah da ya kasance ɗan uwan sa domin da mai martaba da mahaifin tafeedah da yakasance me riƙe da sarautar ɗan malikin maraɗi , ƴa ƴan wa da kani ne uwa ɗaya uba ɗaya . Tun tashin su tare suka tashi tamkar ƴan tagwaye ance sai hali ya zo ɗaya ake abota toh abotar Biyamaradi yousoufa da tafeedah ta ƙaryarta hakan domin idan aka ɗauke ra'ayin su da yazo ɗaya akan karatu da aikin da suka yi haɗakar ra'ayi akan sa ,"watau aikin ɗamara " da ya kasance su dukkanin su sojoji ne sai dai shi tafeedah sojan sama ne , saɓanin yarima yousoufa da yake sojan ƙasa . Bayan hakan kowannen su halayen sa saɓani da na ɗan uwan sa ne , inda Tafeedah ya kasance mutum me barkwanci , surutu da saukin kai, saɓanin yarima yousoufa , hakan ya sa suke yawan samun saɓani akan halayyar juna in da kowannen su yake ƙalubalantar ɗan uwan sa , a ganin yousoufa tafeedah ya cika sakarci da sakewa mutane , yayin da shi kuma tafeedah yake ganin yousoufa a matsayin bauɗaɗɗen mutum miskili marar dadin sha'ani , A tsakanin su ɗaya ya kasa sauyawa ɗaya halayyar sa kamar yadda saɓanin halayyar su sam-sam bata taɓa karfin aminci da abotar su ba ,tun suna yaran su har yanzu da suke kan shekarun girma ,basu da abokan da su ka wuce junan su , duk wasu shawarwarin su tare suke yi , sun san sirrin junan su daɗi da rashin daɗi basa rabuwa duk inda dare yayi idan har suna cikin gari ɗaya ,"aiki bai tura ɗayan su wata jahar koh wata ƙasar ba "toh dare yana yi ka gansu tare koh dai a sashin biyamaradi yousoufa koh kuwa a sashin tafeedah da shima yake bangare guda a gidan su da yake baya kaɗan daga shiyar gidan sarki " sosai abotar su me tsafta ce irin wacce take wuyar samu a wannan zamani " Bayan Tafeedah babu wanda Biyamaradi yousoufa yake so da ƙaunar gani irin karamar kanwar su A'isha wacce ake kira "meram" kasancewar ta (meramar sarki) . ƙwarai Biyamaradi yousoufa yake kaunar meram duk da cewa kanwar sa ce da suke uba ɗaya , domin meram ita ce ƙaramar ɗiya ga hajiya mama ( Saratu ) a cikin ƴaƴan gidan mata ita ce karama , A'isha"meram" yarinya ce ƴar kimanin shekaru sha uku a yanzu tana aji na uku a makarantar gaba da primary . Aisha irin yaran nan ne da gatan da suke da shi bai sa sun lalace da rashin tarbiyyah ba , ta samu tarbiyya sosai a wurin uwar goyon ta "Safiyyah" uwa ga Biyamaradi yousoufa , hajiya umma "kamar yadda ƴaƴan ta suke kiran ta" ita ta ɗauki Aisha tun daga yaye wanda hakan yana da nasaba da ƙaunar da ta ga ɗan ta mafi soyuwa agare ta yana yi wa kanwar ta sa da tun daga lokacin da aka haife ta ya ƙyalla ido ya ganta ,Allah ya dasa masa kaunar ta ciki ran sa fiye da duk sauran ƴan uwan sa ciki har da waɗan da suke ciki ɗaya da shi da su . Lokacin yana matakin farko a jami'ah ai kuwa ya mayar da sashin mama wurin yada zangon sa a duk lokacin da ya dawo daga ɗaukar darasi haka zai kwace aisha daga hannun masu rainon ta yayi ta faman hidima da ita, hakan sam baya yi wa hajiya umma daɗi ganin yadda ɗan ta ya tare a sashin da a da kafin haihuwar aisha sai yayi shekara ma bai taka kafar sa bakin sashin ba " hankalin ta ya tashi akan sanin da tayi cewa garin su baya jiƙuwa a ƙoƙo ɗaya tare da saratu"hajiya mama " Baza ta iya hana yousoufa zuwa sashin hajiya mama kai tsaye ba kasancewar ta san shi kaifi ɗaya ne ,miskilin gaske da ba'a iya sauya masa ra'ayi ta daɗi , hakan ya sa ta bi hanyoyin da take ganin zasu taimaka mata ta dakatar da ɗan ta daga shiga sashin hajiya mama domin tana gudun ta janye mata ɗa tsaf "sanin halayyar saratu "(hajiya mama) " da tayi na tsantsar kissa da siyasa tare da hilatar mutum ya so ta a dole karshe kuma ta cuce sa "macijin sari ka noƙe ce " ( cikin rashin sanin hajiya umma aikin gama ya riga ya jima da gamawa ) Dan haka tayi mata shigar sauri ta bi duk hanyoyin da take da damar bi ya haɗu kuma da ita ke jaan ragamar gidan ta ɗauke Aisha can-cak daga wurin mahaifiyar ta a lokacin tana shekaru biyu a duniya ta dawo sashin ta baki ɗaya , ai kuwa murna gurin yousoufa ba'a cewa kome " yayin da hakan da tayi ya baƙan ta ran hajiya mama sosai amma sai ta boye bacin ran ta. (sanin da tayi ta riga ta gama rarake ƙasan hajiya mama ) Cigaban labari . Yana shiga tamfatsetsen (palourde-parlour )falon nasa ko kafin ya karasa zama akan ɗaya daga cikin kyawawan fararen kujerun da suka sake haskaka falon wayar sa da take cikin aljihun sa ta hau ruri . Ciro wayar yayi daga cikin aljihunn sa tare da tsira mata ido tamkar me nazarin ta ,har sai da ta kusan tsinkewa tukun ya ɗaga gami da yin sallama ya ɗora da faɗin "Comment vas-tu aujourd'hui princesse"? Daga dayan bangaren aka amsa cikin wata narkakkiyar murya " je vais bien Mon amour comment va le travail"? Ya amsa da Alhamdulillah daga haka suka ci gaba da hirar da ake yin ta cike taf da kasaita daga dukkanin bangarorin biyu da shi da wacce ga alamu budurwar sa ce . Idan ɗaya ya furta kalma sai an biyo bayan wasu ƴan ƙananun daƙikai (seconde -seconds) kafin " ɗayan ya bada amsa , inda daga baya ma ya koma budurwar ita ke jaan ragamar hirar, shi daga yayi murmushi sai yace eh ko a ah. Har dai zuwa lokacin da ya sako mata zancen tafiyar sa akan aikin sa har na tsawon lokacin da yake zaton zai iya kaiwa shekara . Nan take ta katse shi tun ma kafin ya karasa yi mata bayani cikin tashin hankali take tambayar sa akan ina lamarin bikin auren su ya kwana ? Wanda ake sa ran zuwan ranar da aka yanke nan da ƴan wasu watannin da suke gaza da uku "lokacin da zata kammala karatun ta" ? Cikin jin haushin tarar numfashin sa da tayi wanda yake ganin kaf duniya yana iya kirga mutanen da suka isa yi masa haka ,yace ke dakata MAIMOUNA lamarin ayki matsayin shi ya wouce douk yadda kike tounani don haka ki ajiye komi a guefe har sai bayan na cimma matsaya bisa aykina. Ko kafin ya gama bayani budurwar da aka kira da maimouna ta fara shishiƙar kuka gama bayanin sa yazo daidai da fashewa da kukan ta bata ko kuma saurarar sa ba ta kashe wayar ta , Ta barshi riƙe da kan waya a kunne , ɗan jim yayi yana son fahimtar abun da ya sanya ta kuka cikin kalmomin da ya furta ,? Rashin gano dalilin ya sa shi ɗaga kafaɗun sa biyu cikin nuna alamar rashin damuwa ya miƙe tare da nufar daya daga cikin fankama-fankaman ɗakunan da suke cikin falon nasa yana shiga ɗaki ya nufi ƙaton window ɗakin gami da buɗe sa a take ƙamshi damina da wata sassayan iskar maraice da ta fi ta ac da yake ɗakin dadi ,ni'ima da sanya nishaɗi ta buso zuwa cikin dakin . Rage kayan jikin sa yayi tare da nufar bayi da alamun wanka yake da niyyar yi ,sai dai wayar sa da ya ajiye gefen gado ta ɗan jaa hankalin sa sakamakon hasken da tayi ,ɗan guntun murmushi yayi ganin sunan princesse da alamar sako a fuskar wayar ,ba tare da ya ɗau wayar ba ya faɗa bayi domin yin wanka. Yana kammala shirin sa ya fito falo jikin sa sanye da uniforme riga da wondo me dabbare-dabbaren kore , ruwan kunkumadi, ruwan madara, da kuma jaa Wanda ko ba'a faɗi ba za'a san kakin soja ne .( Tenue Saharienne ). Da sallama ɗauke akan harcen sa ya sanya kai cikin katafaren Palourdes (falon) mahaifiyar sa wanda yake kama da ɗakin taro "hall" dakatawa yayi daga gefe ya sunkuya tare da kwance igiyoyin jikin takalman sa da suke ɗaure gam-gam da kafar sa har kusan ƙwarin sa , Wucewa yayi niyyar yi (zuwa ciki wurin umma ) bayan ya amsa gaisuwar jakadiya wacce ya tarar tana zaune daga gefe a cikin palourn amma sai jakadiyar ta dakatar shi cikin cewa "Ranka ya dade biyamaradi " yanzu kuwa nake shirin zuwa sashin naka "ta furta hakan tana me satar kallon bayu uku da suke ta faman goge-goge da ƙwal-ƙwale cikin palourn daga can geufe ( umartar su tayi da su kauce su basu wuri ). Gyara tsayuwar sa yayi bayan ya kammala sauraron bayanin bakin jakadiyar , sannan ba tare da ya nuna wata alama! Akan fuskar sa ba ya ce "madallah da ke jakadiyar sarki zan kuma yi taka tsan-tsan tare da sanya ido sosai domin gano gaskiyar wannan zancen da kika zo min da shi , "bayyanuwar wani abu wanda ya sha banban da wanda kika sanar da ni a yanzu " zai iƴa jawo hukunci me tsanani a gare ki dai-dai da yadda doka da shari'a ta tanadar ga masu yin ƙage da sharri , wanda kin riga kin san haka . Daga haka ya juya ya fara tattaki domin nufar wurin mahaifiyar sa "cikin zuciyar sa kuwa cike taf da bakin ciki da baci rai ! Akan labarin da jakadiya ta zo masa da shi game da ɗan uwan sa muhamadou .'mamman" Muhamadou shine ɗa na huɗu a ɗakin hajiya mama "kuma shine ɗan ta ɗaya tal namiji . ****************** Dai-Dai ya sanya kan shi cikin ɗan madaidaicin wurin "da yafi kama da dakin hutawa " ita ma ta kawo kai kiris ya rage su ci gware cikin sauri ta ɗago kai da niyyar buɗe baki amma ganin wanda yake tsaye a gaban ta ya sanya a take ta diririce "tare da yin ƙasa da sauri ta kai gwiwowin ta ƙasa cikin ƴar siririyar murya tace "ina kwana hamma youssouf " , kallon ta yayi na daƙikan da suke gaza da biyar ya ɗauke kansa tare da sake yin kicin-kicin da fuska daga bisani ya wuce yana me amsawa ciki-ciki da lafiya lau " bayan sa ta bi da sassayan kallo daga bisani ta miƙe daga durƙusan da tayi tana me kakkabe gefe da gefen fara sol ɗin rigar da take ɗore bisa kan kayan ta , gyara zaman farin gilashin idanun ta tayi " da saboda firgitar da tayi kiris ya rage ya subuto daga kan siririn karan hancin ta ", Cikin sassarfar yake taku fuskar sa ɗauke da yalwataccen murmushi da yake bayyana ƙatuwar wushiryar da take tsakanin fararen hakoran sa na sama" har ya ƙarasa gefen dardumar da farar dattijuwar take zaune hannun ta riƙe da wani ɗan ƙaramin littafin addini tana dubawa "zama yayi tare da miƙa hannun sa ya kamo nata hannayen da suke ciƙe da awarwarayen zinare da suke ta faman haske idanun me kallon su , ɗaga hannuwan nata yayi dai-dai fuskar sa ya sumbancin bayan hannuwan nata ɗaya-bayan-daya kafin ya sarƙafe dogayen ƴan ƴatsun sa cikin nata yatsun da suke ƙawace da adon jaan ɓakin lalle da yake ta faman sheƙi tare da tashin sassanyan kamshi " Fuskar ta ɗauke da tattausan murmushi take bin duk wani motsin sa da ƙwarar idanun ta zuciyar ta fal! Cike da ƙaunar gudan jinin zuciyar ta "ina kwana ummana kin tashi lafiya ? Yaya fama da jama" ? Allah ya ƙara miki nisan kwana da hakuri da mu umma " cikin murmushi take shafar baƙar kwantatciyar sumar kan sa tana me amsa addu'ar sa da Ameen kafin ta ɗora da tambayar lafiyar sa shima sannan ta ƙara da tambayar sa yayi karin kumallo ? Ƴar dariya yayi sannan "yace umma na makara sai naje officie zan sha café " tana shirin yin magana ta sake shigowa palourdes (falo ) " Bakin ta ɗauke da ƴar siririyar sallama "Budurwar da suka kusan yin karo da biyamaradi ce " Tare da kulawa hajiya umma take kallon ta kafin ta ce yaya kuma kika dawo SIYAMA ? Ke da kike ta mitar kin yi latti , 'cikin inda-inda tare da satar kallon biyamaradi da ya ciro wayar sa yake dannawa "da alama kira yake shirin yi " tace "umm daman umma kamar nayi mantuwa ne , cikin sauri ta juya gami da nufar wata ƴar kofar da take tsakankanin kofofi huɗun da suke cikin wurin "bayan ta hajiya umma tabi da kallo cikin ran ta kuwa tausayi-kauna gami da soyayyar siyama ce taf take kai kawo" Tana shiga ta tura kofar gami da dafe kirjin ta bayan ta jinginu da jikin ƙyauren kofar " a hankali ta juya tare da zamewa ta durƙusa gami da sanya fuskar ta a dai-dai saitin ramin ɗan mukullin kofar , nan take idon ta ya ƙƴallo mata fuskar sa yana hirar sa da mahaifiyar sa hankalin sa kwance in da yake sanar mata da zancen tafiyar sa a cikin kwanaki uku masu zuwa "idan mai martaba ya amince" ɗan jim hajiya umma tayi sannan ta ɗora da cewa wai kou yarona (bata kiran sunan sa saboda sunan surikin ta ne ) shi tahia bisa aykin ba'a iya yin sa ne tare da amre "abun nuhi bai yuwuwa mutun ya tai tare da iyalin sa " ? ... [6/24, 9:49 AM] +234 701 013 7848: Fikrah writers association *MAFARI .........* ( _HARGITSIN RAYUWA_ ) *Umm'muaz* 3 Gyara zama Biyamaradi yayi kafin yace " A zahiri ummana ba wai ba'a tahia akan hidimar aiki tare da iyali bane sam-sam sai dai duba da irin wurin da zan tai ba kasa ta bace ba ,kuma zan tai ne domin kwantar da tarzoma sannan zan jagoranci mutane sama da dubu ɗaya ne ,ni ne shugaba gare su ina bukatar tattara hankalina kachokam na ɗora bisa aykina tare da kula da mutanen da suke karkashi na " Numfasawa yayi daga bisani ya ɗora da cewa kuma"ummana ki yi duba da irin ita Maimuna ɗiyan sarki ce wacce du inda zata ta zauna sai tare da bayun ta masu yi mata hidima , shin ya kamata daga amren mu na douke ta zuwa wata ƙasa a bakin ayki na wurin da babu tabbacin zata samu irin gatan da take samu a gidan su da kuma wanda zata iya samu da ace anan ta zauna da auren mu ? Ummana a duba lamarin nan da kyau ,? Sauke numfashi "hajiya umma" tayi duk zance ɗan nata gaskiya ne aykin sa me tattare da hatsarin rasa rai ne , ayki ne na sadaukarwa ga ƙasar sa ,shi ya sanya tun farko bata so ba youssof ya zaɓi da ya zama soja , so tayi yayi ta karatu me zurfi har ya zama alkali ta yadda du ranar da ya zama shi ne bisa gadon sarauta mulki ba zai taɓa yi masa wahalar gudanarwa ba , Sai dai duba da yadda shi youssof ya ɗage ya tsaya kai da fata kan ra'ayin sa , ya sanya daga karshe ita da mai martaba suka tsaya masa wurin ganin cikar burin sa bayan kammala karatun jami'ar da ita ma da rarrashi da ban baki youssof yayi "domin da farko so yayi yana kammala karatun gaba da primary ya fada makarantar horar da sojoji " sai dai mai martaba yayi masa jaan ido sosai sannan ya yadda yayi karatun jami'a inda ya karanci fannin sociologue" yana fitowa kuwa ya miƙa takaddun sa ga neman shiga soja , nan take kuwa aka ɗauke sa "kasancewar sa ɗan manya" cike da so da kaunar aikin sa gami da nuna tsantsar ƙwazo ya fara aykin wanda hakan ya jawo nan take ya fara taka matakan nasara hawa hawa , sau biyu ana sawa da shi a cikin zaɓaɓɓun sojijin da ake turawa kwantar da tarzoma a kasashen ƙetere "kasar Somalia da Libya " cikin ikon Allah kuwa duk tawagar da yake jagoranta lafiya suke dawowa cike kuma da tarin nasarori " hakan ya bashi ɗaukaka a cikin ƙanƙanin lokaci har ta kawo sa ga matsayin da yake kai a yanzu wanda a karo na uku sai ga shi an sake tura shi ƙasar Nigeria domin yaƙi da ƴan tawayen Boko haram " Cikin yanayi marar daɗi yake kallon fuskar mahaifiyar sa wacce da alama tayi nisa cikin tunani "shi ya san daga mai martaba har umma basa son aikin sa "kuma da yana da iko tabbas da ya haƙura da aikin amma toh shi yaya zai yi ne shi ya tabbatar haka Allah ya halicci zuciyar sa da ƙaunar aikin soja "domin baya mantawa tun yana shekaru biyar yake ƙwalafaci tare da mararin ganin sa riƙe da bindiga sanye da kakin soja haka ya tashi ya tsinci kansa kullum wayewar gari da mafarkin ya zama soja "abun a jinin sa yake " Muryar sa ce ta doki dodon kunnuwan ta tare da dawo da ita daga duniyar tunanin da ta lula "ummana a cigaba da yi mana addu'a kamar yadda aka saba da iznin Allah babu abun da zai faru da mu sai Alkhairi sannan shekara kamar kwana ce tamkar yau zaki ga ɗan ki ya dawo , ya karashe zance yana dariyar tsokana ". Ƴar dariya itama tayi kafin ta ce addu'a muna kan yin ta yarona kuma insha Allah zamu cigaba fatan mu Allah ya kiyaye tare da shiryar mana ku a duk inda kuke da sauran ƴaƴan musulmai baki ɗaya , to yaya ita ɗiyar tawa da fatan ka sanar mata da batun tafiyar duk da cewa ma nasan idan har tafiyar takasance mai martaba da kansa zai tada ɗan aike zuwa Birnin Agades ɗin " ta ɗora da sake tambayar sa, yaya ɗiyar tawa ta aminta dai kou batare da ta tayar da hankalin ta ba ? Gimtse fuska biyamaradi youssof yayi kafin ya ɗora da mun gama magana kuma ta fahimta , cikin ransa ! Kuwa mamakin yadda wannan lamari zai tafi a haka karfi da yaji yana namiji umman sa ta dunga nunawa da lalle ne ya yi abun da maimouna take so , Sau tari hakan ya sha faruwa hatta akan tsarin ginin gidan sa da aka yi duniya guda daga can Babban filin da yake karshe a cikin masarautar maimouna ita ta zaɓi irin ginin da take so kuma irin sa sak aka yi , ya rasa gano dalilin haka , Shi shine namiji shine shugaba tayaya za'a dunga gwada masa sai abun da matar da zai aura ta zaɓa shi zai yi ? Miƙewa yayi yana me duba agogon hannun sa cikin sauri yake yi wa umma sallama "Ummana ni zan wuce ina ga yau zan iya kaiwa cikin dare kafin dawowa ta sabadda yau zamu fara zuwa bakin bodar da ta haɗa mu da Nigeria domin duba irin tsaron da za'a fara ajiyewa ta wurin" , Bin sa da ido hajiya umma take "tana lure sarai da sauyin da aka samu akan fuskar sa tun da ta ambaci sunan maimouna "cike da so ta fara kwarara masa addu'a tare da sake jaddada masa ya kula da kan sa sosai , har zuwa lokacin da ya karasa ficewa daga wurin da take ", Sauke ajiyar zuciya tayi a lokacin da ya bacewa ganin ta ,lokaci daya ta ɗauke fuskar ta daga jikin bulin makullin kofar tare da miƙewa tsaye ta juyo fuskar ta wacce take " ɗauke da wani tattausan murmushin da a zahiri yake nuna zuciyar ta na cikin annashuwa " dan tsalle tayi tare da juyi kafin a hankali ta motsa laɓɓan ta cikin cewa " za'a ɗaga bikin auren hamma youssouf har zuwa nan da wata shekarar me zuwa ,' taku ta fara yi a hankali da ya dangana ta da jikin katafaren gadon da yake rufe ruf da kyakyawan labulen da iskar da take busowa daga jikin tagar ɗakin yake ɗan kaɗa shi a hankali " janye labulen tayi tare da zama a bakin gadon " ɗan rangwaɗa kan ta tayi cikin cewa "ɗaga ranar bikin hamma youssouf yana nuni da nasarar da na kan iya samu ,hakan yana iya yiwuwar samun wata sabuwar dama a gareni "., Lokaci ɗaya ta gimtse fuska domin tunowa da tayi da nisan da hamma youssouf ɗin zai yi mata wanda ya sanya ba shiri ta ji hawaye ya cika gurbin idanun ta ","hamma youssof zai tafi Nigeria har na tsawon shekara , zan rabu da ganin sa na adadin kwanaki ɗari uku da sittin " bazan iya ba " zuciyata zata iya samun matsala kafin cikar adadin kwanakin nan ya zama dole na samowa kai na mafita " ., zabura tayi jin ana ƙwanƙwasa mata kofa ,' Cike da jin haushi ta ce "waye a nan ? Cikin ladabi hadimar da take durkushe ta bakin kofar tace '"Allah ya huci zuciyar uwargijiya ta sako ne daga " Babbar uwa (hajiya umma ) tace a sanar da ke lokaci yana tafiya " ., ɗan jim tayi kafin ta amsa kina iya tafiya gani nan fitowa ., ki fito lafiya ranki ya dade,' Miƙewa tayi tana me jin duk fitar ta yau ta fice mata daga kai "tana da tabbacin yau bata iya tsinana wani abun kirki a wurin aykin ta "saboda chakuɗuwar farin ciki tare da bakin ciki ! A lokaci guda cikin ran ta ,' Sake ɗurkusawa tayi har ƙasa tana me daɗa yin sallama da hajiya umma wacce ta kafe ta da ido tana me yin nazarin ta ", har ta miƙe da shirin tafiya ta ji hajiya umma ta sake kiran ta "yaki nan ɗiya ta ', dawowa tayi tare da sake durkusawa ", babu dai wani abun da yake damun ki koh ? Da murmushi ɗauke akan fuskar ta ta ɗago tana me kallon fuskar mariƙiya gareta matar da a da take mata ganin mahaifiya tun tasowar ta domin bata taɓa cin karo da wani abu wanda zai sanya ta kokonto akan zaman hajiya umma mahaifiyar ta ba ,' har sai da lokacin da ta shekara goma sha bakwai(ta kammala makarantar gaba da primary ) a lokacin ne hajiya umma ta shaida mata hakiƙanin gaskiyar matsayin ta a wurin ta "hakan kuma ya samo asali ne dalilin ƙin amincewa ta bi mahaifin ta na ainahi da tayi ," da ya nemi son tafiya da ita wurin sa tayi hutun kammala karatun gaba da primary da tayi ", yazo da buƙatar tafiya da ita gidan sa domin ta ga sauran ƴan uwan ta da ya haifa tare da matar da ya aura bayan rasuwar zainab ", Sosai a ranar tayi kuka ,kukan maraicin ta kafin a hankali ta hakura ," ta bi mahaifin ta , ta kuwa ji daɗi sosai da wannan hutun da tayi tare da kannen ta da matar mahaifin ta da ta kasance matar kirki ,' Sai dai tun bayan dawowar ta daga gida (daga wurin mahaifin ta ) ta tarar da hamma youssof shima ya dawo daga jami'a inda ya kammala karatun sa ,' Rana ɗaya ta tsinci yanayin ƙaunar da take masa a zuciyar ta tana sauya muhalli ,daga so irin na ƴan uwan taka zuwa wata irin zazzafar soyayyah ,' ta aure wanda take jin idan har bata mallaki hamma youssof a matsayin mijin auren ta ba zuciyar ta kan iya samun babban raunin da zai iya dangana ta da kushewar ta ", Gyaran murya hajiya umma tayi bayan ta gama nazarin ta sosai ta ce "siyama ki kasance me tsananta addu'a a koyaushe akan dukkanin lamuran ki kin ji koh ? Gƴaɗa kai siyama tayi ,' to maza tashi ki je ɗiyar Albarka Allah ya tsare min ke ya dawo da ke lafiya ," cike da jin daɗi da wata irin kakkarfar soyayyar mariƙiyar ta siyama take amsawa da Ameen "umman mu" Alherin Allah ya isar miki umman mu" , Tsaf hajiya umma ta gama gano abun da yake nuƙurƙusar zuciyar ɗiyar ta siyama ,'domin tun ba yau ba dai take lure da duk wani motsin Siyama akan youssof ɗin ," a kuma bangare guda na zuciyar ta lamarin sosai yayi mata daɗi ganin yadda yayi kicibus da tsohuwar niyyar da ke kulle a cikin zuciyar ta akan siyama da youssof ɗin tana da tabbacin baza ta samu matsala daga bangaren siyama ba". Damuwar ta akan youssof ɗin ne wanda tun farko ta lura youssof ɗin bai wani cika kula lamarin siyama ba tun suna yara "kusan ma za ta ce jinin sa bai ɗauki siyama ba domin tun suna yara kullum faɗan sa da yayar sa 'ubbo' akan siyama ne ,' yana dukan siyaman kasancewar ta yarinya me tsinannen rawar kai a lokacin kuruciyar ta ,"shi kuwa youssof mutum ne marar son hayaniya hakan yasa garin sa bai jiƙuwa ƙoƙo guda da na siyama 'nan take zai bige ta ' wanda hakan yake haɗa sa faɗa da yar tasa domin duk duniya idan aka ɗauke hajiya umma da mahaifin siyama na ukun su a ƙaunar siyama ubbo ce ,sam bata ƙaunar abun da zai taɓa siyama ,' sosai take gwadawa siyama soyaƴyah da gata fiye da ƴan uwan ta da suke ciki guda ma, ' har dai zuwa lokacin da ubbo tayi aure a birnin Niamey gidan ta shine wurin hutun siyama a duk lokacin da ta samu hutun makaranta ,har kuma yanzu da siyama ta kammala karatun ta a shekaru biyu da suka gabata daga Université médecine- medical school ( makarantar horar da likitoci ) in da ta karanci fannin likitar haƙora ( Dentiste-Dentist ) ta kuma fara aiki a asibitin gwamnatin tarayya ta ƙasa reshen jahar maraɗi watanni sha tara da suka wuce , siyamar bata da zancen da ya wuce wurin da zata rubuta hutu musamman ta je da ya wuce gidan addar ta ta ubbo ,wacce mijin ta a yanzu ɗan majalisar tarayyah ne na ƙasa baki ɗaya ," A lokacin da youssof ya zo tare da batun ya samu matar aure a shekarar da ta gabata "dai-dai lokacin da ita kuma take gaf da fiddo manufar ta na son haɗa youssof da siyama aure ta shaida ga mai martaba "wanda ta san zai fi kowa farin ciki da wannan lamarin sanin da tayi lokacin marigayiya zainab tana raye suna da kyakyawar mu'amala ita da mai martaba duk kuwa da cewa shi mai martaba ya girmewa kanwar ta sa da tazara sosai domin mutane uku ke tsakanin sa da marigayiya zainab " , sai dai kuma youssof ɗin ya riga ta tada maganar auren in da yazo da murnar sa yake sanar mata da samar mata da suruka da yayi,' tun a lokacin ta so ta rusa maganar ta kuma fiddo masa da ainahin nata ƙudirin na son haɗa su aure shi da siyama,' Sai dai jin wacce ɗan nata yake da zummar aurowa a matsayin surukar ta ya sanya ta yin laƙwas "ba wata bace wacce youssof ɗin zai auro illah maimouna ɗiya ga mai martaba sarkin AGAƊES , Maimouna ita ce ɗiyar sarkin agades mace ɗaya tal 'ƴar da ta samu gata da kulawa irin na bada kwatance .' Maimouna kyakyawar yarinya "ƴar buzaye" wacce ake kwatancen kyaun ta har ta kai sunan ta da kyaun ta ya shiga jerin abun kwatance a bakin al'umma " haka za'a ji budurwa idan ta ƙure wanka da gayu za'a ji masoyan ta na kururutata " wance kin kou ga kan ki sai kace gimbiya maimouna '? " ko kuwa idan budurwa ta cika feleƙe da yanga dan ita ɗiyar masu akwai ce nan za'a ji ƴan adawar ta suna faɗin" yo ai mu munga gimbiya maimouna ma karshen gata dai kenan" a taƙaice dai gimbiya maimouna ɗiyar gata ce gaba da baƴa , Sanin duk wani wanda ya kwan ya tashi ne cikin ƙasar Niger ", Sarautar birnin Agades shi ke da suna har karfin mulki fiye da dukkanin sauran manyan masarautun gargajiya da ke ƙasar Niger , sanin hakan da hajiya umma da mai martaba sarkin maraɗi suka yi ya sanya nan take zuciyoyin su suka cika da farin ciki ganin ɗan su zai auro ɗiya mafi soyuwa ga Sarkin agades ", wanda sun san hakan ba ƙaramin babban nasara tare da samun sabuwar ɗaukaka gare su da ma jahar maraɗi baki ɗaya ba ne ," Nan take hajiya umma ta ajiye zancen auren siyama da youssof a gefe wanda a da take jiran kammaluwar karatun ita siyama sai ta tado maganar kuma a wancen lokacin siyamar ta riga ta kammala karatun tun watanni biyar da sun ka wuce ", jinkirin da aka samu na son ta sake tsananta addu'ar neman zaɓi ne sai kuwa ga shi jinkirin ya zama Alkhairin da ya sa dole ta ture maganar siyama gefe ba kuma domin ta hakura ta janye zancen baki ɗaya bane "sawun giwa ne ya take na rakumi "sannan cikin ranta tana maimaita ai youssof mijin mace huɗu ne ", da wannan ta ajiye batun gefe , tare da bayyana tsantsar farin cikin ta da batun maimouna , Cikin satin mai martaba sarkin Maraɗi Abdoul-azizou Baskore ya tura da takardar neman aure ga sarki Usoumanu Ibrahim tounouss na birnin Agades , koh da sakon ya isa ga Mai martaba sarkin Agades shima ya bayyana farin cikin sa bayan da yaji ta bakin ɗiyan sa , in da ta tabbatar masa da amincewar ta tare da sake jaddada yawan ƙaunar ta ga biyamaradi youssofa, anan take mai martaba sarkin Agades ya bada tukuici mai yawa tare da takaddar jaddada amincewar sa ," Bayan dawowar ƴan aike daga birnin Agades a daren mai martaba sarkin Maraɗi ya gana da hajiya umma inda yake sanar da ita tayi magana ga ɗiyar ta siyama cewa a tare za'a haɗa bikin ta da na youssof dan haka ta tsaida guda cikin masoyan ta ," Anan hajiya umma bata yi ƙouron baki ba ta sanar da mai martaba haƙiƙanin shirin zuciyar ta tun daga farko ', Ɗan jim mai martaba yayi bayan kammala jin dukkanin kalaman uwargidan sa ," sosai yaji daɗin kyakkyawar niyyar ta sai dai yadda ta ture Al'amarin bayan bayyanuwar maimouna ya sanya shi jin wani iri tamkar dai akwai sautin son kai cikin lamarin nata ," sai dai yayi saurin kauda zargin daga ransa akan sanin da yayi a duniya idan ana kirga masoyan siyama hajiya umma tana daga sahun farko ƙwarai yana alfahari da ita akan irin kyakyawan riƙon da tayi wa ƴar kanwar sa , " dan haka yace idan har ita siyama ta amince da shi youssof ɗin ya zama dole ga youssof ya auri siyama a matsayin matar sa ta biyu shekara guda bayan auren sa da maimouna idan Allah ya yadda ", Nan take maɗaukakin farin ciki ya bayyana akan fuskar hajiya umma ,' tana mai sake jaddada masa da ƙaunar da ita siyama ta lura tana yi wa youssof ɗin tun shekarun baya ," nan dai mai martaba ya tsaida batun auren siyama da youssof sai dai ya nemi hajiya umma da ta bar batun nan a tsakanin su ,"saboda gujewa ƴan kai-kawo ', . *Mairambiri Borno Nigeria* Hasken ranan da ta ɗago ta fara ɗan zafi ita ta sanya ta fara motsi , kafin ta buɗe dogayen manyan idanun ta da suke farare tas tas , da sauri ta miƙe daga kwanciyar da take a cikin taɓon da ya cakuɗe da ruwan da ya kwanta a cikin ƙonanne ɗakin nasu wanda wuta ta riga ta ƙona azaran saman ɗakin ," da sauri ta fara lalube gefe-da-gefen ta , jin bata ji almun mutum a ɗakin ba ya sa ta miƙe tsaye ta fara laluben hanyar fita tare da kiran sunan ƴar uwar ta "yakaka "yakaka " santsi ne ya kwashe ta suuu ta tafi ta faɗi dabas a bakin kofar ," bayan ta ya bada ƙara ƙaƙas , " wani kuka ne ya taho mata a lokacin da wani mugun tsoro ya ɗarsu a ranta koh dai ƴan tawayen boko haram sun dawo ne jiya ? Sun tafi da yakaka ," tunanin hakan ya sa taji wani karfi ya zo mata ta yunƙura da karfin ta ," ta miƙe ta fara tafiya a cikin ruwan da ya cika tsakar gidan nasu da ƙasa bata kai ga shanye sa ba ', Cigaba tayi da ƙwalla kiran sunan yakaka ' yakaka ' yakaka , ruwan hawaye yana me cigaba da ambaliya akan fuskar ta da karfi take jefa kafar ta ba tare da tana laluben gaban ta ba burin ta kawai ta tafi neman ƴar uwar ta ɗaya da ta rage mata," ji tayi ta kaiwa bango karo tayi taga-taga ta tafi da baya ta sake faɗuwa," da gudu take jin takun tahowar mutum kafin taji sautin muryar ta itama cikin firgici tana ƙwalla kiran sunan ta 'falmata 'falmata falmata' Da gudu ta shigo gidan ,"wurgi tayi da ledar da take hannun ta tare da ƙarasawa gurinta zuwa lokacin ita ma kokarin tashi take tana mai sake kiran sunan "yakaka ', ɗago ta tayi tare da rumgume ta cikin jikin ta ,' itama kamkame ta tayi ," kafin su dukkanin su biyu su saki juna suna masu haɗa baki gurin tambayar junan su,' "Falmata baki ji ciwo ba koh ? Yakaka ina kika je babu abun da ya same ki koh ? Banji ciwo ba yakaka ina kika tafi kika barni kin sa hankalina ya tashi kar ki sake tafiya ki barni yakaka ,"falmata ta furta hakan tana me laluben fuskar yakaka ," Hannun ta kai gami da share mata hawayen da suke gudu har yanzu akan ƙuncin ta ,"kafin cikin ƙarfin zuciya tace kiyi hakuri kanwata lokacin da gari ya waye naji wucewar mutane ɗai ɗaya hakan ya sa na lallaɓa na leƙa anan naga wani mutum shi ɗaya da gudu zai wuce shine na bishi nima ina tambayar sa koh ya ake ciki a gari ," shine yake gaya min shi hanya ce ta biyo da shi ta nan ƙauyen mu ,'daga ƙaramar hukumar Bama yake ," a yau suka wayi gari da afkawar ƴan tawayen boko haram a yanzu haka sun farma ƙaramar hukumar Bama suna ta kisa ,"irin dai yadda suka yi anan jiya ", mutumin ya tabbatar min da gwara na gudu domin ƴan tawayen boko haram zasu iya dawowa su mamaye dukkanin ƙauyukan da suke tsakanin Bama da Konduga tun da sun riga sun mamaye garin bama ", na tambaye shi to ina zamu ? Shine ya ce min ance wai a cikin Birnin Maiduguri gwamnati ta tanadi wurin da mutane irin mu ƴan gudun hijira zamu zauna a kula da mu kafin a yaki ƴan tawayen boko haram ," Tashi mu tafi falmata kar mutumin nan ya yi mana nisa kin ga mu ba mu san hanyar Maiduguri ba bamu taɓa zuwa birni ba ," zame hannun ta da yakaka ta kama tayi kafin cikin muryar kuka ta fara cewa "yakaka ni babu in da zan tafi , yakaka ba mu san inda su mama suke ba , idan muka tafi kuma su mama suka dawo neman mu fa ? Mu zauna yakaka mama zata dawo neman mu zata dawo ta tafi da mu inda ta ɓuya ," Share ƙwallar idon ta tayi kafin ta ce falmata su mama fa su ma sun tafi Maiduguri suna jiran mu a can ," da zasu dawo ai da tun jiya zasu dawo idan muka zauna anan koh ƴan tawayen boko haram basu kashe mu ba wuya da yunwa da kishirwa zasu kashe mu ," miƙa hannu tayi ta kamo baƙar ledar da ta shigo da ita wacce take yawo akan ruwan da yake tsakar gidan ," kin ga wannan ma tsintowa nayi a hanya wata kaza tana ta so ta fasa ledar ta kasa shine na bita na ƙwace" biredi ne a ciki ki ƙarba ki ci mu tafi falmata," ta karasa zancen da sigar rarrashi ," ******************** Hannun su sarƙafe da na juna suke tafiya ," bayan sun fito daga gidan nasu kowaccen su tayi shiru da abun da take saƙawa a cikin ran ta . A hankali yakaka ta waiwaya tana me kallon kofar gidan su ," sosai ta tsirawa gidan ido tamkar me son kirga adadin yawan bulon da akayi amfani da shi wurin ginin gidan ," gizo idanun ta ya fara yi inda ta hango mahaifin ta ya fito kamar yadda ya saba hannun sa riƙe da hular sa , gefe guda ita ce a tsaye hannun ta riƙe da buhun su na zuwa gona daga bakin kofar kuwa mahaifiyar su ce tana ɗaga musu hannu kamar dai yadda ta saba ," hawayen idanun ta ne suka gangaro gami da ɗiga akan kafar falmata ɗan jijjiga hannun ta da yake cikin na yakaka falmata tayi kafin ta ce mu tafi mana yakaka," Mu tafi falmata cewar yakaka wacce ta ke bin dukkanin ginin unguwar su da kallo hotunan al'amuran da suka gudana tun daga tasowar ta a cikin unguwar suna ta wucewa ta cikin tunanin ta ," wata irin kewar mahaifarta tana mamaƴar ta tana jin tamkar ta tafi kenan ," tana jin tamkar karshen ganin ta da gidan su da garin su kenan ," gefen zuciyar ta tana jin wani sabon karfi tare da karban sabon sauyin da rayuwa ta zo mata da shi ,"yayin da take jin nawin girman da ya hau kan ta na rike kan ta da kanwar ta falmata yana kama ta,' sai dai tana jin kome runtsi da Wahala zata kula da falmata ko da ita zata rasa rayuwar ta," miskin falmata ," Taku Falmata ta fara yi tana me jin yadda duhu yake mamaye zuciyar ta kamar dai yadda duhun yake a zahiri a idon ta ," tana jin duk wani farin cikin da ta san ta samu daga lokacin da tayi wayo zuwa yau yana barin jikin ta ,' wani irin ƙunci yana mamaye cikin ran ta ," tana jin kuncin yana ƙaruwa da dukkanin wani takun ta guda ɗaya da take yi da niyyar barin garin su mahaifar ta , zuciyar ta tana cike da tsoron sabuwar rayuwar da zata fuskan ta alhalin tana makauniya a garin da bata da kowa bata san kowa ba sai ƴar uwar ta ," tsoro sosai ya ɗarsu a ranta " , sai dai wani sashi na ranta yana faɗa mata zata dawo watarana , wataran zata dawo garin su mahaifar ta , zata sadu da mama da sauran kannen ta ," bata san lokacin da wani matsanacin kukan da yake cike da tsoro da kuncin zuciya ya kufce mata ba ,' kuka take bilhaƙ ," Matsa hannun ta yakaka take yi alamun rarrashi domin a zuwa yanzu ita ma bata da karfin zuciyar rarrashin falmata domin tana da tabbacin tana buɗe baki kukan zuciyar da take yi zai bayyana a zahiri ," ita ma bukatar rarrashi take tana bukatar matallafin da ko da ba zai taimaka mata da kome ba ," zai furta mata kalmar ZAKI IYA YAKAKA, Hanyar da mutumin nan ya gwada mata ita su yakaka suka kama," suna tafe basa jin motsin kowa sai kukan tsuntsaye ," ɗan turus yakaka tayi ganin hanyar bakin jeji sosai ta kawo su ," jin sun tsaya ne ya sanya falmata wacce ta fara gajiya tace yakaka har mun kawo Maiduguri ne ? Cikin sanyin murya yakaka tace falmata gani nayi hanyar da muke tafiya a kan ta ta kawo mu bakin jeji ," jin batun jeji ya sanya falmata sake cukumo rigar yakaka tare da cewa mu koma kawai yakaka ," na faɗa miki daman kar mu taho ," Jin takun tafiya tare da hayaniya kamar har da kukan yara da suka ji shi ya sa su saurin juyawa " wasu gungun mata (sun fi su goma ) tare da yara da namiji guda ɗaya suka hango ," bisa ga dukkan alamu su ma a jigkace suke daga su sai kayan jikin su ," wucewa suka yi ta gaban su ba tare da sun ko kula da su ba ," cikin sauri yakaka ta saki hannun Falmata tare da cewa ", bari na tambayo su koh su ma maiduguri suka nufa ," da ɗan gudu ta cimma su saboda saurin da suke zabgawa cikin harshen su take tambayar su ," ko maiduguri za su ?" Ba tare da sun waiwaye ta ba ɗaya daga cikin su ta bata amsa da ",Eh ", Da gudu ta koma baya gami da kamo hannun ƴar uwar ta tana jaan ta tare da cewa zo mu tafi falmata mun samu abokan tafiya waɗan nan mutanen su ma maiduguri suka nufa ,' ita dai falmata bata ce ƙala ba ta bi yakaka suka faɗa jeji tare da bin bayan mutanen nan da har sun fara yi musu nisa cikin duhun ciyawa ," Doguwar tafiya suka yi sosai cikin ƙungurmin dajin nan da yake cike da itatuwa da ciyayi gami da ƙayoyin da suke ta faman huda musu takalman su suna sukar kafafun su, ba sa cewa ƙala a tsakanin su ," har zuwa lokacin da rana ta ɗan gota tsakiya alamun azahar ta yi ", namijin ciki shine ya basu umarnin tsayawa a dai-dai wani wurin da ruwan sama ya ƙwanta yayi kamar ƙaramin kududdufi " , cewa yayi a huta a sha ruwa sannan ayi sallah a cigaba da tafiya ," Yaraf ,'duk suka zazzauna wasu ma kwanciya suka yi warwas a ƙasa ,kallo ɗaya za'a yi musu a fahimci tsabar gajiya da yunwa a tare da su ," yaran ciki kuwa daman tuntuni suke kukan yunwa da kishirwa dan haka ko da su ka ga ruwan nan , nan take suka nufi wurin wasu suka sa tafukan hannayen su biyu suna ɗebo ruwan suna sha wasu kuwa bakin su suka sa a kan ruwan suna sha ", Yakaka da falmata suna cikin waɗanda su ke shan ruwan da hannayen su ,ɗauro Alwala su ka yi bayan sun sha ruwan ," su ka kuma jira sauran matan su ma su ka zo sha ruwan tare da ɗaura alwala ," namijin ya jaa su jam'i haka a cikin dajin ," Ƙarar wucewar wani abu me tsananin karfi da matsanancin ƙara da yake barazanar kashe musu dodon kunnuwa shi ya sanya a firgice ! Su dukkanin su, su ka ɗaga kai sama ba tare da sun sallame sallar da su ke ba ," yaran ciki kuwa nan take su ka fasa kuka tare da ƙanƙame iyayen su Shawagi wannan abun da wasu daga cikin su , su ka ce "jirgi ne " ya cigaba da yi ," yayin da su kuma su ke tsaye carko carko , kawukan su a ɗage suna hango jirgin da yayi ƙasa ƙasa da har su ke iya ganin launin sa da yake koren kala , ruwan madara da kuma ruwan hanta "(coffee)," Falmata lalubo hannun yakaka tayi tare da riƙe ta gamgam cikin karkarwar murya tace yakaka menene shi jirgin ? Basu yi aune ba kawai su ka ji an saki wani abu kamar bom ," wanda ya faɗo kurkusa da mutumin nan da yake jagorar tafiyar su tare da wasu mata biyu da suke tsaye ,' nan take su ka tarwatse jinin su ya watsu a jikin sauran su ," wani irin kururuwa su ka yi a tare da yake nuna tsantsar firgicin su ," karo suka fara yi da juna cikin gigicewa suna masu neman hanyar gudu jin yadda jirgin nan ya sake sakin wanna abun da basu kai ga fahimtar harsashi ne ko kuwa bom ?," Fisgar hannun Falmata, yakaka tayi wacce take ta faman waige-waige tare da ihun tambayar yakaka me yake faruwa ? Ba tare da yakaka ta bata amsa ba ta fisge ta cikin ihun kukan da ƙarar jirgin nan ya dusashe ƙarfin sautin take cewa mu gudu Falmata idan ba haka ba zamu mutu ," Takawa su ke da matsanancin gudu suna jefa ƙafafun su wanda ko takalma babu "domin basu samu damar sanya takalman su ba " wurin da duk suka tsinci kan su nan suke jefa kafa basa duba gaban su bare su waiwaya baya ,"wasun su kuka da ihu suke yayin da tsiraru daga cikin su suke addu'a ," gudun ceton rai suke cike da tsananin tsoro tare da tashin hankalin jin kamar ƙarar jirgin nan na bin su  ," Cikin tsananin gudun da su ke ne yakaka taji hannun falmata da take riƙe da shi gam-gam suna gudun tare ," hannun ta ya fisge daga cikin nata lokaci guda kuma taga falmata tayi ƙundubala ta tafi gaba ɗaya ta faɗi ta gaba fuskar ta ta bugu da ya sa ba shiri ta saki wani irin ihun azaba tare da ƙwalla kiran sunan Allah ," Cikin kaɗuwa yakaka wacce har ta yi gaba saboda matsanancin gudun da suke ," ta dawo da baya da gudu gami da durƙusawa ta tallafo falmata wacce hancin ta da bakin ta ke fidda jini ," sai dai wata ƙarar da falmata ta sake saki a lokacin da yakaka take koƙarin ɗago ta ya sanya babu shiri ita ma yakaka ta fashe da matsanancin kuka ," Falmata sannu Dan Allah ki tashi " ta furta hakan tana me gogewa falmata jinin da ya bata mata fuska da ɗankwalin kan ta da ta zame lokaci guda kuma tana me ɗaga kanta sama tare da yawata idanun ta a sararin samaniya cikin tsammanin ganin jirgin sojojin nan ," Ƙafata yakaka ƙafata ta maƙale a rami wayyo Allah na yakaka zan mutu ," Falmata ta furta hakan a lokacin da ta ruƙo ɗayar ƙafar ta, take ƙokarin zaro ƙafar daga wani ɗan ramin da yafi kama da na "ƙurege" ko kuwa dai kananun dabbobi dangogin sa ", Cikin tashin hankali yakaka ta sake fuskar falmata gami da miƙewa ta koma ta wurin ƙafafun ta ,"kokarin zaro ƙafar ta fara yi ,"idanun ta suna zubar hawayen tausayin kanwar ta da ya sa ta kusan mance halin tsaka mai wuyar da suke ciki ," A gigice ta ɗago kan ta ganin wani hannun da tayi ya kama kafar falmata "cikin taya ta kokarin zaro kafar ," Ɗaya daga cikin abokan tafiyar su ce ," ita ma yarinya ce wacce zata iya girmewa yakaka da kadan ", Da karfi su ka samu nasarar fusgo kafar falmata wanda hakan ya sa yakaka tayi faɗuwar ƴan bori akan ciyawar farar ƙayar da ta soki bayan ta ya sa ba shiri ta sake zabura ta miƙe gami da rugowa ta ɗaga kafar falmata wacce tayi futu-futu da ƙasa," ta ɗora akan cinyar ta ,"lokaci guda tana tambayar falmata kafar bata ji ciwo ba koh ," ? Yakaka kamani na tashi mu gudu," Falmata ke furta hakan a lokacin da take laluben hannun yakaka fuskar ta tana bayyana tashin hankalin da take ciki ," da sauri yakaka ta miƙe bayan ta sauke kafar falmata daga jikin ta ,"yunkurawa tayi tare da ɗago ta ," ganin haka ya sa yarinyar da take tsaye a gefe tana kallon duk abun da suke ta matso gami da kai hannu ta kamo ɗayan hannun falmata da nufin taya yakaka ɗaga ta ," Wani irin zamiya falmata tayi tare da warce hannun ta daga jikin yarinyar wanda hakan yayi sanadiyar komawar su ƙasa da ita da yakaka ,a lokaci ɗaya ta kanƙame jikin ta wuri guda tare da cewa ," Yakaka waye a wurin nan tare da mu ? Aljanu ne koh ? Falmata wacce ta taya ni muka zaro kafar ki daga rami ce ɗaya daga cikin abokan tafiyar mu ........," ****************** Kika ce kin san hanyar Birnin Maiduguri Yagana ? Tambayar da yakaka ta jefawa Yagana (abokiyar tafiyar su ) kenan lokacin da suke cigaba da tafiya ," sai dai saɓanin ɗazu yanzu a nutsen su suke tafiya ,"samun nutsuwar su ya samo asali ne daga fahimtar da suka yi jirgin nan ya tafi ya daina bin su ," Sai dai fa a yanzu zuciyoyin su cike take taf da tsoron ganin su uku ne rak a ayarin tafiyar su sauran duk sun watse kuma basu sake cin karo da ko guda daga cikin mata takwas da kananun yara biyar ɗin da suka rage a ayarin nasu a bayan mutuwar namijin cikin su tare da mata biyun ba ", Eh nasan maiduguri yakaka mun taɓa zuwa tare da yaakura na ( yayar mahaifiyar ta ) Sau goma kuka taɓa zuwa koh sau ashirin ," da a yanzu kika ce zaki mana jagora ? cewar falmata wacce take ɗingisa kafar ta gefe-da-gefen rigunan su ita da yakaka a ƙulle da na juna ,. Sau ɗaya dai na taɓa zuwa tun lokacin ina shekaru biyar na taɓa yin rashin lafiya wai wasu kuraje suka fito min shine aka ce sai a Babban asibitin cikin Maiduguri za'a ban magani ," ta karasa zancen tana me ɗaga zanin ta zuwa gwaiwa ," kin ga taɓon kurajen nan yakaka wannan tabon da kike gani tun ina shekaru biyar a duniya," Waiwayawa su ka yi jin Falmata ta jaa ta tsaya lokaci guda suka dawo gefe da gefen ta suka tsaya ," yagana tana cewa kin gaji ne falmata ? Falmata wani wurin yana miki ciwo ne cewar yakaka ? Fashewa da kuka tayi cikin shishiƙar kuka ta fara cewa yakaka sai da na faɗa miki kar mu taho kar mu taho kika ce sam sai mun taho ," kika nace ," gashi nan yanzu zamu mutu a cikin daji kura ta samu na kalaci ," ta karashe zance tana jaan majina . Shiru yakaka da yagana suka yi domin a hakiƙanin gaskiya su dukkanin su biyun karfin hali kawai suke domin kuwa ƙarƙashin rayukan su cike yake taf da tsoron duhun daren da ya riga ya fara shigowa ne,"alhalin suna cikin ƙungurmin dajin da basu san gabas ba bare yamma ," Kiyi hakuri Falmata ni bana son yawan kukan nan da kike kin san dai baki da lafiyar idanu ," muyi ta addu'a kawai Allah yana tare da mu ," cewar yakaka Eh Falmata addu'a ita ce mafita kuma ina jin kamar ma mun kusa isa maidugurin dan ina tunanin lokacin da aka kaini asibitin kamar ance wai bamu kwana a hanya ba wai awanni bi...... Ke ni dallah ki mana shiru ,"ke idan ana zancen waɗan da suka taɓa zuwa birnin maiduguri ma har kya sako baki ? Wucewa gaba Falmata tayi a fusace tana lalube a ranta kuwa tana ayyanawa kome ta fanjama . [6/24, 9:58 AM] +234 701 013 7848: Fikrah writers association *MAFARI.......* ( _HARGITSIN RAYUWA_ ) *umm'muaz* 4 Ƙanƙame da juna suke kwance a ƙarƙashin duhuwar bishiyar kukar da duhun ta ya haɗu da duhun dare tare da na damina ya bada matsanancin duhun da ba'a ko iya ganin tafin hannu . Falmata ce a tsakiyar su yakaka da yagana suna gefe-da-gefen ta ,ko ƙokkwaran motsi basa iya yi saboda tsabar zullumi da tsoron da ya cika musu rai ! Numfashi ma a sace suke yin sa yayin da kunnuwan su suke tarwai a buɗe daga jin motsin abun da yake nesa da su da kusan rabin kilomita . Babu motsin kome a dajin da ya wuce kukan jemagu da kuma wasu ƙananun ƙwarin da ba'a iya tantance kukan su ," haɗi da wani kuka da suke ji daga nesa ƙadan da su wanda tsananin tsoron da suke ji ya sa suka kasa tantance kukan koh na menene ,"ya dai fi musa kama da kukan bijiman sa (shanu) sai kuma jifa-jifa kukan manyan namun dawa waɗanda suke nesa sosai daga wurin da suke . Ƙasa-ƙasa muryoyin su suka fara tashi ," Umm Yakaka zan yi fitsari ," Fitsari kuma falmata dan Allah kiyi hakuri mu jira safe. Falmata kawai kiyi fitsarin nan anan kwance a jikin mu ," cewar yagana Motsin da suka fara ji mai ɗan karfi yana doso inda suke ne ya sanya su sake damuƙar junan su kafin jikin su ya ɗau karkarwa kar-kar-kar . Shikenan muryoyin su sun jawo mu su . Wani ɗumi yakaka da yagana suka ji a jikin su wanda yake tabbatar musu yawaitar motsin da suke ji tare da ƙarin gabato su da motsin ke yi shi ya sanya falmata sakin fitsarin da tace tana ji saboda tsabar tsoro Haske suka fara hangowa wanda basa raba ɗaya biyu hasken tocila ne ," kafin su fara jin taƙun kafafun mutum ," tare da tashin muryoyin mutanen da baza su wuce biyu ba sai dai magana suke a cikin yaren da su yakaka basa fahimtar sa ," Gani suka yi an ɗan kau da hasken tocilan kafin su ji an taho har kurkusa da su ," karar zubar wani abu kamar ruwa ne ya fara sauka kunnuwan su kafin su ji ruwan mai ɗumi ya fara fallatsuwa akan fiskokin su a zaɓure suka miƙe zaune wanda a tunanin su koh ruwan zafi ake watsa musu ," Miƙewar da suka yi shi ya mutumin da yake tsaye shima ya zabura tare da yin eho a take kuma ya buɗe murya gami da yin magana da maɗaukakiyar murya cikin yaren sa nan take sai ga hasken tocila ya dallare fuskokin su yakaka ," ***** A tsugunne suke bisa gwaiwowin su tamkar mai laifi a gaban hukuma ," maza ne kimanin goma a zagaye da su dukkanin su hannun su rike da makamai kama tun daga kan ,sanduna , gatari ,takobi,kwari da baka , wuƙake , da ma bindigar harbi ka buya , Fahimta da suka yi su yakaka basa jin yaren su na hullanci ya sanya ɗaya daga cikin su ya juya harce cikin yaren hausa Yaro ku su waye ? Kuma daga ina kuke cikin daren nan ? Nan take yagana wacce da alamu ta fi su yakaka fahimtar hausa ta ce mu ƴan gudun hijira ne daga garin Bama nake waɗanan kuma "tana nuna su yakaka " abokan tafiya ta ne daga nan kauyen mairambiri suke ," ƴan tawayen boko haram ne suka tarwatsa mana garuruwan mu ," Duk bayanin nan da suke yi yakaka da yagana basu samu damar ganin fuskokin su waye a tsaye zagaye da su ba su dai sun san mutane ne , kuma a ƙalla sun ji saukin tashin hankalin da suke ciki akan sanin da suka yi ashe akwai mutane dayawa haka kurkusa da su ,". Juya harshe wannan mutumin da ya tambayi su yakaka yayi ,"tare da yi wa abokan tafiyar sa fassarar bayanin da yagana tayi cikin yaren su na hullanci ," nan take hayaniyar su ta ƙaure a wurin da alama Tausayawa yaran suke tare da Allah wadai da ƴan tawayen boko haram wanda sun riga sun san da zaman su ," kuma tsakanin su da su babu kare bin damo "abun nufi ko da sun haɗu cikin daji basa shiga harkar juna ," ( Makiyaya da ƴan tawayen boko haram ) Bayan doguwar muhawarar da suka yi a tsakanin su nan mutumin ya juya ga su yakaka yace ": Yaro yanzu ku ina kuka nufa ? Maiduguri zamu ," ance gwamnati ta tanada mana wurin zama ', za'a kula da mu cin mu da shan mu sutura da wurin kwana har ma ance za'a samu a makarantun gwamnati ," abincin cin mu ma na.... Katse ta mutumin yayi : Yaro kun san hanyar Maidugurin ne ? Nan falmata wacce take fahimtar mafi yawan kalmomin nasu ," mayar da magana cikin hausar ne ke yi mata wahala , Tayi tsagal tace Baba wallahi bamu san hanya ba", dan Allah ku taimaka ku kai mu Maiduguri dan Allah ta karashe zancen tana matsar ƙwallar wahalar da ta ciko mata ido," Yaro zamu taimaka muku amma mu ba Maiduguri muka nufa ba ," mu daga nan ikko muka nufa ,"amma zamu raka ku har inda muke ganin kun wuce hatsari sai mu gwada muku sauran hanyar ," nan wurin da kuke akwai hatsari sosai , Juyawa ya sake yi suka yi magana da ƴan uwan sa ," sannan ya juyo tare da cewa ku biyo mu ," Lumshe matsakaitan idanun ta tayi lokacin da ɗumin madarar saniyar sabuwar tatsa ya sauka a cikin ta ," dago kan ta tayi daga cikin ƙoƙon da yake cike taf da madarar ta maida kallon ta ga fuskar kanwar ta wacce tayi kasaƙe hannun ta rike da nata ƙoƙon da bata tunanin ma ta kai bakin ta ," idanun ta suna sheƙin ruwan da ya taru a cikin su a tsaye idanun na ta suke ƙem wuri guda ," da alamar tayi zurfi cikin tunani ," a hankali taga ƙwallar da ta taru a gurbin idanun nata sun silalo da gudu sun sauko bisa ƙuncin ta ," da sauri ta ajiye ƙoƙon madarar ta gami da ƙarasawa inda falmata take zaune akan wani ɗan dutse ," dire gwaiwowin ta tayi a ƙasa lokaci ɗaya kuma ta sanya hannu gami da goge mata ƙwallar da suke cigaba da fitowa Yakaka yau kwanaki biyu kenan muna wayar gari ba tare da iyayen mu da sauran ƴan uwan mu ba ," Allah ya jikan Baba ya gafarta masa ,"insha Allah shi mutuwa hutu ce a gareshi ," To amma yakaka mama fa da sauran kannen mu a wane hali suke ciki ? Wataƙila suma ƴan tawayen boko haram sun kashe su irin yadda suka yi wa Baba ," idan kuwa har suna raye tabbas mama tana cikin mawuyacin halin da ya fi wanda muke ciki a yanzu ," Yakaka muna shiga birnin Maiduguri abu na farko da zamu fara yi shine neman maman mu ," Ƙai hannunta tayi ta lalubo fuskar yakaka jin tayi shiru bata cewa kome duk bayanin da take yi , nan taji ruwan hawayen da suka faca-faca akan fuskar ta ," share mata hawayen tayi kafin a hankali ta kai kanta ta ɗora akan kafaɗun ƴar uwar ta , idan ke kika yi kuka a halin yanzu ni me kike so nayi yakaka ? ,kiyi haƙuri ki daina kuka insha Allah zamu haɗu da maman mu ," Nemo yatsun hannun falmatan tayi ta sarƙe su cikin nata hannun "falmata ba ina kuka bane a domin wahala koh raunin zuciya akan halin da muke ciki ba," ina kuka ne akan tunanin halin da mama da ƙannena suke ciki ina kuka akan wahalar rayuwar da kike ciki a halin yanzu alhalin bani da karfin taimakon ki ,"dubi kafar ki falmata ta ɗago kafar falmatan da take ɗaure da ɗankwalin ita yakaka," Duk ƙafar ta soke da kayoyi daga idon sawun ƙafar kuma a kumbure yake in da ta faɗa rami a jiya ," Falmata tun tasowar mu ban taɓa ganin ciwo irin wannan a jikin ki ba ,"duk da cewa muna rayuwa cikin talauci amma iyayen mu suna tattalin mu ,da lafiyar mu" amma ki duba daga shekaranjiya zuwa yau da rikon ki ya dawo kaina na gaza wurin baki kulawa gashi duk kin ji rauni ," sai nake ganin laifin kaina da zan iya falmata da goyon ki zan yi nasan da mama ce da ta sauke Bulama ta goye ki amm dubi ni ... Ɗago kan ta tayi tare da toshe mata bakin ta da hannun ta ," fuskar ta babu walwala tace yakaka daga yanzu ki daina ganin laifin kan ki akan duk wani abun da kaddara zata ɗoramin ," Sannan ki daina ganin kamar ni a dalilin bani da ido bazan iya yi wa kaina kome ba ," wasu abubuwan zan iya yakaka ,"a yanzu rayuwa ta sauya min ta inda nake ganin dukkanin wasu abubuwan da a baya bazan iya su ba a cikin sabuwar rayuwar da zamu fuskanta zan iya su ," abun da nake so kawai kar ki taɓa ɗauke matsayin ki na wacce take gaba da ni a koyaushe kika ga zan faɗa rami ki taro ni kin ji yakaka ? Naji Falmata sai dai nima ina son ki bar min matsayina na yayar ki a duk lokacin da na nuna cewa nice gaba da ke wurin baki kulawa ,"kin ji koh ? Ɗan siririn murmushi tayi " naji yaa yakaka ," A hankali yagana ta sanya babban ɗan yatsan ta, ta ɗauke ƙwallar da ta gangaro mata daga cikin ido ," tana tausayin kan ta sosai da sosai tun tasowar ta kasancewar ta tashi ne ba tare da mahaifan ta ba mahaifiyar ta rasu tun tana yarinya yayin da mahaifin ta ya tafi ci rani ,"tun tana shekaru goma har yau bai dawo ba "dan haka a hannun kakar ta mahaifiyar Baban ta ta girma" sai dai daga jiya zuwa yau ta sake tausayawa kan ta a sanadin ganin tsaftatatciyar soyayyar ƴan uwan taka da take gudana tsakanin yakaka da falmata , wanda ya sa ta fahimci ba ƙaramin gibi take da shi a cikin rayuwar ta a sakamakon rashin dan uwa koh ƴar uwa da take da shi ba ," sosai soyayyar da ta lura tana gudana a tsakanin ƴan uwan biyu ta birge ta tare da bata sha'awa . Ajiye ƙoƙon ta"wanda ta riga ta shanye madarar ciki tas " tayi a gefe tare da miƙewa ta nufi wurin da har yanzu yakaka da falmata suke zaune ,"sai dai saɓanin ɗazu yanzu a jere suke a zaune inda falmata ta matsawa yakaka ta zauna a gefen ta suna fuskantar mahuɗar rana da ta fara ɗagowa tana keto tsakankanin ciyayin , ranar ta bada wani haske mai kyau ," Dafa kafaɗun su tayi da hanun ta ɗai ɗaya ," idan an gama tattaunawar sirrin tsakanin ƴan uwa a tashi mu tafi mu mayar musu da ƙoran nasu kafi su gama shiri su fara jiran mu kuma ,"kun san dai sun ce da wuri zamu kama hanya saboda miƙaƙƙiyar tafiyar da ke gaban mu ," murmushi yakaka tayi ," yagana baki da dama ," Satar kallon falmata yagana tayi wacce ko alama bata nuna ma taji abun da yaganan ta ce ba ," Kamo hannun falmata ," yakaka tayi da sauri yagana ta zagayo tare da kama mata ɗayan hannun ,"amma ga mamakin su sai ji suka yi tace "zan iya tashi da kaina ,! Yunƙurawa tayi amma sai suka ga ta kai hannun ta gami da lalubar hannun yakaka ta rike gam gami da miƙewa a hankali ,"hakan da yagana ta gani ya sa ta fahimci falmata bata so ta ita ta taimaka mata sai ƴar uwar ta "ɗan tabe baki tayi cikin nuna ko oho ", ***** To kun ga nan shine karshen dajin konduga daga nan ai gashi kuna iya hango gidajen da suke ta cikin yankin unguwannin Birnin Maiduguri ,"wadancen gidajen da kuke iya hangowa daga nan suna cikin unguwar da ake kira dalori ne , kuna ƙarasawa can kun riga kun shiga birnin Maiduguri ," mu daga nan muke sake komawa mu ɗauki hanyar in da muka nufa ," wannan dogon bayanin yana fitowa ne daga bakin bafullatanin mutumin nan ,"bayan sun kawo su yakaka iyakar dajin yankin konduga da cikin garin maiduguri ," Nan take su yakaka suka durkusa akan guiwowin su suna masu jero godiya da tarin addu'o'i ", zuciyoyin su kuwa ƙwal kamar an musu bishara da wani babban abun Alkairi," Da murmushi ɗauke akan fuskokin fulanin nan su biyar "da alama sun baro sauran a daji tare da dukiyoyin su (shanun su ) suke amsa jerun gwanon addu'o'in su yakaka ," kafin mutumin ya ɗora da cewa toh yaro sai ku kula da kan ku sosai ,maiduguri babban gari ne sosai domin haka sai kun yi taka tsantsan da kome , da mu ƴan gari ne da zamu sanya ku a hannun wasu da muka sani to mu ma bamu san kowa ba cikin maiduguri," Sanya hannun sa yayi a aljihu ya zaro wata tsohuwar naira ɗari biyu ya damƙa a hannun falmata wacce ya lura bata gani ," daga haka suka yi musu sallama tare da juyawa suka ɗau hanya abun su ba tare da sun sake waiwayawa ba ," Shirun dakikai biyu zuwa uku ne ya gitta tsakanin ƴan matan uku bayan juyawar fulanin zuwa inda suka fito ,"ga su dai ga birnin maiduguri bayan doguwar tafiyar da suka yi na kimanin kilomita 74-76, akan kafafun su daga ainahin garuruwan su , da kuma tarin ƙalubale da hatsarin da suka shiga a yayin tafiyar ," wanda ya kamata ace a yanzu da maɗaukakin farin ciki za su durfafi birnin na maiduguri , to sai dai a halin yanzu da fulanin nan suka juya tare da tafiya suka bar su a faffaɗan fili sararin Allah da ya tafi ɗoɗar daga nesa suna hango gidajen jama'a da fulanin nan suka tabbatar musu gidajen cikin birnin maiduguri suke ," sai duk suka ji zuciyoyin su sun raurawa ,'akan tunanin ina kuma suka dosa ? Ina zasu nufa ? Falmata ce ta katse shirun nasu a yayin da ta tattaro gutun yawun bakin ta da ya gama bushewa a sakamakon ranar damina da aka bude a yau ", Yakaka tsayuwar me muke yi ne kuma ? Kamata yayi mu ƙarasa cikin garin mu fara da neman maman mu a yau ɗin nan kin ga idan Allah ya sa muka ganta kafin dare ,"yau baza ta shiga cikin lissafin ranakun da zamu ƙara kwana ba tare da ita ba ko kuwa ? Mukut ! Yakaka ta haɗiye guntun yawun da ya saura mata a baki ," Falmata a yadda fa nake hango girma da yawan gidajen da suke cikin Birnin Maiduguri ya sha banbam da irin na garin mu" amma dai bari mu ƙarasa mu gani ," Yunkurawa suka yi tare da kama hanyar suna tafe babu me cewa ƙala ," sun yi tafiya me ɗan tsawo zuwa lokacin da suka fara cin karo da gidajen da suke farko-farkon unguwar dalori Qaurters . Ware ido sosai yakaka tayi tana kallon tsarin gidajen tare da yawan mutanen da ta gani suna ta kai kawon su ," nan take taji zuciyar ta buga da tunanin ina zasu fara bi su nemo mahaifiyar su a cikin wannan faffaɗan birnin ? Ta bangaren yagana kuwa yawan jama'a da tsarin gine-ginen , bai wani zama baƙon abu ba a saboda babu laifi garin su "Bama" shima babbar Alkarya ce wacce take cike da Al'umma da kuma cigaba dai-dai da zamani ," tunanin ta ya fi karkata ga inda zasu je su samu mafaka kamar yadda kafin su fito daga gida a lokacin da labarin shigowar ƴan tawayen boko haram ya baza garin su aka fara guje guje da ƙokarin barin garin ɗaya daga cikin ƙannen mahaifin ta shi ya basu tabbacin idan suka tafi birnin maiduguri akwai mafaka agaresu da musamman gwamnati ta tanada ," Dan haka take taku zuciyar ta cike da son ganin sun isa mafakar ta su ," Ga bangaren Falmata kuwa ita ba ganin garin take yi ba amma hayaniyar muryoyin jama'a tare da ƙarar wucewar ababen hawa da suka cika mata kunnuwa sun isa sanar mata cewa ta shigo wani wuri da ya sha bamban da mahaifar ta me rangwamen hayaniyar jama'ah , ƙarar ababen hawa kuwa sai ranar cin kasuwar garin su take iya jiyo su daga nesa-nesa ," nan take taji tsoro ya kamata sakamakon tunowa da tayi da fannah ƴar makotar su wacce mota ta taɓa bigewa ta karya mata kafafu " , nan take ta lalubo jikin rigar yakaka ta haɗa da jikin tata rigar ta sake ƙullewa ," sannan ta sake jefa hannun ta cikin na yakakar wacce ita ma ta rike hannun falmatan gam-gam . Cikin mutuwar jiki suke tafiya a lokaci guda yunwar da take ƙwaƙular cikin su tana tuno musu da rabon su da sanya wani abu a cikin su tun madarar da suka sha da safe ga shi dai yanzu azahar ta yi domin suna iya jin kiran sallah daga massalatan da suke cikin unguwar,"Yakaka idan muka samu wurin da ake sayar da abinci mu tsaya mu saya kafin mu isa ga masaukin mu ," Uhm yagana wane masauki kike zance a yanzu bayan duk alamu sun bayyana a garemu bamu da hanyar da zamu bi ta sada mu da gidan gwamnatin ,"idan kuma kina da hanyar sai ki faɗa ," cewar falmata , Yagana Jaan bakin ta tayi ta tsuƙe domin ta lura ba wani birge falmata take yi ba a kome ," a gefe guda kuma na zuciyar ta ,tana me gaskata zancen falmatan tabbas , ganin kitse take yi wa rogo a duk zaton ta suna tako kafafun su cikin garin maiduguri zasu tadda jami'an da aka ce suna bada tsaro ga mutanen maiduguri zasu chafe su ,tare da sada su da masaukin su cikin farin ciki da walwala ," Sai dai tabbas a yanzu tana iya hango yiwuwar sauyawar tunanin ta "wanda ya sanya ta hango kanta a matsayin wacce tayi masauki a kan bola " da hakan ya sanya ba shiri ta fara zare idanu tana kallon mutanen da ta lura su ma a halin yanzu kallo suke bin su da shi a duk inda suka gifta . Duk ba wannan ba yanzu abun da yakamata mu fara yi shine mu samu wuri muyi sallah daga nan sai mu fara tambayar mutane hanyar masaukin da kika ce an tanada ga irin mu ,"koh me kuka ce ,"Yakaka ke furta hakan bayan ƴar gajeruwar muhawar da taji falmata da yagana suna yi , Cigaba suka yi da kutsawa cikin unguwar suna neman wurin yin alwala har dai suka yanke shawarar tsayawa a dai-dai wata mahaɗar da ta fi kama da tashar tsayuwar motoci saboda yawan ababen hawan da suka gani a wurin ,"sai dai yawan masu saye da sayar a wurin kama tun daga kan masu ɗanyen kaya ,da masu kayan abinci na awu ,"har ma zuwa masu saida dafaffen abinci da kuma masu toye-toye , ga kuma ƴan tebura nan dangin su masu saida biredi da sauran su ya sanya su hasashen ƙila kasuwa ce," tsayawa suka yi a wurin suna rarraba idon neman wurin da zasu samu damar Alwala , Daga gefe kaɗan da su , suka hango masallaci wanda rumfar kwano ta kare gaban sa mutane suna ta Alwala wasu kuwa sun kammala alwala suna sallolin su a cikin rumfar ," Ɗan yawatawa da idanun ta yakaka tayi tana neman ruwan Alwala ,"sai dai yawan idanun da ta gani akan su ya saka ta cikin firgici ,"kusan illahirin mutanen wurin hankulan su da idanuwan su akan su yake ," kuma idan ba idanun ta suke mata ƙarya ba kusan duk mutanen wuri ɗaya suke kallo a jikin su", daga kan kirjin su zuwa cikin su ,'! A hankali ta sauke idon ta tabi inda suke kallo a jikin su ta gani koh wani abun ne a jikin nasu ," Hannu ta kai tare da gyara wuyan rigar ta da ya ɗan saɓule lokaci ɗaya kuma tana kai hannu ta gyarawa falmata ita ma nata wuyar rigar , duban ta 'ta mayar kan yagana wacce ta fahimci ita ma ta lura da irin kallon rashin yaddar da illahirin mutanen wurin ke bin su da shi ," Ƙasa tayi da muryar ta "yagana kin lura da irin kallon da mutanen nan ke bin mu da shi ? Koh daman haka mutanen birni ke yin kallon su ? Ina lure da su nima ,"amma ina ga haka suke kallon su "dan yaakura na tace a lokacin da ta kawo ni asabitin tsatsareni da ido likitan nan yayi a cewar ta saura kaɗan ta ɗauke ni mu tafi dan tayi zaton ma koh karama ne (maye ) ɗan guntun tsaki ta jaa a lokacin da suka haɗa ido da wani matashi majiyi karfi yana kallon su tsakar ka, lokaci ɗaya kuma yana danna wayar sa tare da kara ta a kunne "," Jibe shi dan Allah ya wani tsare mutane da ido toh kurwar mu kur ," Falmata kawo kuɗin nan na ƙarasa can na sayo mana ƙosai da doya nan wurin ma jama'a sun yi yawa mun ƙara gaba kawai muyi sallar ," Falmata bata ce ƙala ba ta miƙa mata gudar ɗari biyun da take duƙunƙune a hannun ta "sashi guda na zuciyar ta! Yana gaskata mata zancen su yakaka na cewa da suka yi an zuba musu ido domin kuwa ita ta riga su sanin ana kallon su ,dan tun da suka nufo wurin jikin ta ya bata akwai wani abun cutarwa ko kuwa idanun mutane akan ta ,'duba da yadda taji tsikar jikin ta tana ta faman miƙewa,'hakan shine alamun da ita take fahimtar akwai matsala a wuri "baiwar ta kenan" , a gefe ɗaya cikin ranta kuwa cike fal! Da haushin yagana akan yadda take nuna ita fa ala dole ta fi su sanin maiduguri Alhalin kuwa su da ita duk sammakal tilo ," basu da wani bambanci. Taku biyu yagana ta yi suka fara jiyo tsuwwar wani abu wanda basu san ko meye bane ,"yayin da hankalin su ya kasu biyu ɗaya akan mutanen da suka ga sun fara guje guje wasu ma har suna barin kayayyakin sana'o'in su ,gefe guda na hankalin su na ga kan tsuwar nan da suke ji tana sake durfafo inda suke , so suke su fahimta akan wannan tsuwar ne mutanen ke gudu koh kuwa meye dalili ,? Yakaka ƙarar meye ne wannan ɗin kuma meyasa naji kamar takun gudun mutane ?falmata ta furta hakan a dai-dai lokacin da take lalubar jikin yakaka tana gyara ƙullin da ya haɗa bakin rigunan su 'da alamun shirin gudu take " Nima ban sani ba Falmta," Yunƙurin buɗe baki yagana take cikin cewa wani abu amma sai maganar ta maƙale mata a fatar baki.' sakamakon ganin manyan motocin da suke ɗauke da irin fentin da suka gani a jikin jirgin saman nan da yayi musu ɓarin wuta a daji ," a take suka fahimci ƙarar nan da suke ji daga jikin motocin nan take fitowa . Ɗurum dum ,"bugun sautin zuciyoyin yakaka da yagana a lokacin da suka yi idanu huɗu da tarin motocin da suke da tabbacin na waɗannan mamallakan jirgin saman ne ,"shikenan mun mutu mun lalace yakaka , shikenan wallahi sun biyo mu ne su kashe mu ," Su waye suka biyo mu ? Yagana wai meke faruwa ne ,"cewar falmata da maganganun yagana suka yi mugun ruɗa ta ," Sojojin da suka biyo mu da jirgi a daji sune gasu nan a mota .... Sauran maganar maƙalewa tayi a fatar bakin yagana a lokacin da ta ga gungun sojojin nan suna durƙowa daga bayan manya manyan motocin su hannayen su duk riƙe da bindigogin su da ya sanya cikin yagana ba da wani sautin ƙululu lokacin da tayi arba da su ,"wannan fa shi ake cewa anyi gudun gara an tadda zago ," Jeruwa sojojin suka yi daga nesa kaɗan da inda su yakaka ke tsaye a sandare ko numfashi da ƙyar suke jaa ," Da gudu wani soja ya fito daga cikin gaban wata mota hannun sa riƙe da wata jibgegiyar bindiga ," ɗaga ta yayi gami da jaan kunamar bindigar ƙaraƙat ,'ya saita ta akan su yakaka da zuwa yanzu suke ta ɗigar gumi kamar an tsamo su daga rafi ," Remove your clothes all, " Sasarai su dukkanin su suka yi suna wulwulga idanu cikin rashin sanin takamaimai ɗin abun yi lokaci guda kuma tsoro ya sake cika zuciyoyin su a sakamakon lura da suka yi cewa duk yawan mutanen wurin nan a yanzu basu ga ko mutum guda ba daga su sai sojojin nan ,"ji suka yi zuciyoyin su na barazanar faso kirjin su ., Fahimta da sojojin nan suka yi su yakaka basa jin turanci ya sa ɗaya daga cikin su ɗaga murya ", Ku cire kayan jikin ku idan ba haka ba zamu harbe ku mu kashe ku ," Cikin tsananin firgita yakaka da yagana suka kalli juna lokaci ɗaya suka ji falmata ta rushe da kuka ," Ji suka yi an sake daka musu tsawa Zamu harbe ku idan kuka sake minti ɗaya ," Ba shiri yagana ta fara cire tun daga ɗangalallen hijabin ta har zuwa rigar ta da yanzu take kan cirewa ," Satar kallon yagana ,"yakaka tayi kafin cikin rawar jiki ta miƙa hannu tana warware kullin da yake tsakanin rigunan su ita da falmata lokaci guda tana me cewa falmata ki cire kayan ki idan ba haka ba zasu kashe mu ,: Tsaye suke daga su sai siket din ciki hannayen su rumgume da kirjin su ,fuskokin su kuwa shaɓe shaɓe da ruwan hawayen da ya chakuɗa da majina gami da gumi ," Magana sojojin suka yi a tsakanin su bayan sun gama ƙare musu kallo Daga wurin da suke ," Sir I think they're not Boko Haram girls , there was no bomb in their bodies," ( shugaba ina tunanin waɗan nan. ba ƴan matan boko haram bane , babu nakiya a jikin su ) Yes they're not , (ƙwarai ba su bane ) Daga inda sojan nan ya yake tsaye ya sake ɗaga murya tare da basu umarni su sanya suturun su ," Koh kafin ya ida rufe bakin sa har sun yi nisa wurin sanya kayan nasu ,"tsayawa suka yi suna jiran su sake jin umarni na gaba ,"idanuwan su kuwa basu bar zubar ruwan hawayen wannan tozarci da tashin hankalin da suke ciki ba ," ba ma dai kamar falmata wacce har karkarwa take tsabar kuka ," Gani suka yi ɗai ɗaya da ɗai ɗaya suna komawar su cikin motocin su ,"yayin da suka ga waɗan nan biyu da suke yi musu magana ɗaya da hausa ɗaya cikin yaren da basa fahimtar sa sun nufo inda suke bindigogin su saɓe akan kafaɗun su ," Suna ƙarasowa wannan me jin hausan yace musu ", daga ina kuke kuma ina zaku ? A wannan karon shiru yagana da ta kasance jaa gaba wurin mayar da amsa tayi tana zazzare idanu tare da satar kallon bindigogin hannun su ," Jin yagana tayi shiru ya sanya yakaka ta buɗe bakin ta cikin maƙyarƙyatar murya tare da gurbatatciyar hausar ta tace ", :Umh daman mu ƴan hijira ne daga garin mu shine-shine muka zo nan neman gwamnati ta taimaka mana da masauki ," Inane garin naku ? Ƙauyen mairambiri Magana sojojin nan biyu suka yi a tsakanin su cikin harshen turanci ," Ku zo mu kai ku camp mu ajiye ku saboda idan kun cigaba da yawo haka a gari mutane baza su yadda da ku ba a karshe ma ana iya yi muku dukan tsiya da tunanin ku irin ƴan matan da boko haram suke ɗaura musu nakiya ne , su shiga cikin kasuwa koh taron jama'a su yi ƙunar baƙin wake ," bayanin da sojojin nan suka yi musu kenan bayan sun gama shawara a tsakanin su Nan fa aka shiga kallon-kallo tsakanin yakaka da yagana ," camp ina ne camp ?koh dai gidan horar da mutane ne sojojin nan zasu tafi da mu ? Wannan ne zancen da yake ta kai kawo cikin zuciyoyin su dukkanin su uku lokaci guda kuma suka ji wata sabuwar nadama baki daya ta kama su ,"daman haka mutanen cikin birni suke azzalumai haka kawai sai su hau jibgar mutum ? Tsawar da aka daka musu ita ta sanya ba shiri yakaka ta kama hannun falmata suka bi bayan sojojin nan da su har sun yi juyawar su sun kusa isa ga motocin su tun bayan da suka basu umarni ," Wani irin mahaukacin gudu motocin sojojin nan suke akan tsakiyar titin na Maiduguri ," duk inda suka gifta motoci da sauran ababen hawa darewa suke suna basu hanya ," Tsugunne su yakaka suke a bayan hilux ɗin, sojoji biyu sun sanya su a tsakiya a zaune a kan ɗan tudun da aka tanada domin zama ," ji suka yi iskar shaƙa ta musu yawa a saboda gudun da motar ke yi ,"nan take maƙoshin su ya bushe ƙemas , idan ban da sharar hawaye babu abun da suke yi ,tun da suka hau motar babu me cewa ƙala ," Gware yakaka da falmata suka yi ," a sakamakon wani irin birki da motar da suke ciki ta jaa," wani marayan kuka falmata ta fashe da shi a dalilin zafin da ya ziyarci ƙwaƙwalwar ta a dalilin gwaren da suka yi ", Dira sojojin da su ke tare da su a bayan motar su ka yi kafin su yi musu umarni akan su sauƙo , Tsayawa yakaka-da-yagana suka yi suna ƙarewa wurin da aka kawo su kallo ,"wata babbar kofa ce a gaban su me kama da kofar gari a ganin su, sai da ƴaƴan hanjin cikin su yakaka ya kaɗa sakamakon ganin wasu gungun sojoji da suka yi daga cikin wata rumfa a gefen kofar ," Yakaka ina aka kawo mu ,? Inji falmata ," Nima ban sani ba falmata ,amma dai kamar wani babban gari ne shima gashi dai har da wata babbar kofar sa ," ta furta hakan tana me satar kallon sojojin da koh kula da su basu yi ba," Ku zo mu je nan shine camp (sansanin ƴan gudun hijira ) inda gwamnati ta tanadar ga ire-iren ku ," a cewar wannan sojan da ya wuce gaba ," Da sauri su ka bishi ransu yana wani ɗan motsin daɗi-daɗi ! Duk da cewar dai basu gama aminta da zancen sa ba domin basu tabbatar ba ,' Yakaka da yagana su na sanya kafa cikin wurin suka fahimci ba ƙaramin babban fili bane ta ciki , a yayin da suka fara yawata idanun su zuciyoyin su cike da mamakin ganin mutane birjik fululu iyakar ganin su suna ta harkokin su ," Hayaniyar jama'ar da falmata ta fara ji yana tashi cikin yaren su , shi ya sanya ta ji kaso goma na tsoron da yake cike da ranta ya kau ,! Bayan ƴar gajeruwar tafiyar da suka yi , bakin wani gini sojan nan ya tsayar da su yayin da shi ya taka ya shiga cikin ɗan wurin mai kama da ɗaki ,"(Office)" bai kai minti biyar ba ya fito ba tare da yace da su kome ba yayi wucewar sa cikin rashin kulawa da gaisuwar da wasu mutane maza da suke zaune turmus a cikin ƙasa da suke yi masa ," Cigaba da tsayuwa su yakaka suka yi a wurin har dai zuwa lokacin suka fara jin ƙafafuwan su sun fara sagewa a gefe guda yakaka da yagana cikin ransu suna nazarin tsarin wajen ," daga gefe gine ne a jere reras tamkar ɗakuna da barandar su doguwa wanda aka yi ginin da bulok tare da rufin kwanon da suke iya hango rufin sa da duk rana da ruwa suka gama illata sa ya zama jazir ," babu abun da yafi yawa a sararin wurin irin bishiyoyin darbejiya wanda suka lura karkashin kowacce bishiya a cike yake da mutane maza waɗan da suke zazzaune wasu kuma a kwance ,yayin da wasu suke a kishingiɗe turmus a cikin ƙasa ," daga inda suke tsaye suna iya hango matan da suke cike a cikin kowanne ɗaki har zuwa barandar ,' dukkanin su mata ne da ƙananun yara da kallo ɗai-ɗaya su ka yi musu suka fahimci halin tagayyara da wahalar da suke ciki ( makamanciyar ta su ), Daga farfajiyar wurin da babu wadatar bishiyoyi wasu manyan ɗakuna ne wanda aka yi su da ƙarafuna tare da rufin leda mai nawi ,"tantinan wucin gadi ", nan ma a cike yake da mutane maza da mata ," wata boyayyar ajiyar zuciya yakaka ta sauke lokacin da taga wasu maza sun zo sun wuce ta gaban su ,"hannun su riƙe da buhun-hunan da ta gane na abinci ne , Yakaka wai tsayuwar nan kam ba ta ƙare ba ce koh ? Yagana ke furta hakan a lokacin da ta karya gwaiwar ta da nufin tsugunnawa , "sai dai bata kai ga tsugunnon ba taji ɗaya daga cikin mutanen da suke zaune karkashin bishiya daga gefe ya ce ," kai kai ku tashi daga nan chan za ku tafi ku nemi wurin zama," yana yi musu nuni da sashin ɗakunan nan. " koh kafin yagana ta samu abun faɗi ,"suka ga an fito daga wannan ɗan ɗakin da daman suke dakon jirin fitowar mutum daga cikin sa ," da sauri suka zube ƙasa suna gaishe da ɓakin jibgegen mutumin da yake yi musu kallon sheƙeƙe ," Ba tare da ya amsa gaisuwar ta su ba ya fara cewa to menene ,? Menene kuma ? Kai Duba ni fa na fara gajiya da ku da ƙorefe-korefen ku , ku koma can daga wurin ku idan waɗanda Alhakin faɗa musu ƙorefe ƙorefen naku ke wuyan su , sun zo kuna iya zuwa kuyi dafifi ku faɗa musu , amma nikam bazan iya wannan halayyar taku ta rashin godiya ba ," wuce su yayi tinƙis-tinƙis yana tura cikin sa tare da mita ,"haba ace mutane sam baku da godiyar Allah a ɗau nawin ku ci da sha da gurin kwana ba tare da koh sisin kobo ba amma duk da haka kullum ta Allah sai kun zo da sabon tsirfa ,"yau ku ce wance gobe wannan koh da yake ba laifin ku bane ," gwamanati da ta ƴanta ku daga noma da shan ruwan kududdufi ita ke da laifin ", An ɗauki tsawon mintuna biyu babu wacce tace ƙala tsakanin su ukun , kowacce da abun da take saƙawa cikin ran ta ," Yaraf ,"yakaka ta ƙarasa bajewa a ƙasa daga durƙuson da suke ," a sakamakon bangaje ta da wata mata tayi wacce take tafe tana ta zabga sauri har zanen ta na kuncewa bayan ta kuwa wasu mata ne su ma gungu sun doshi wajen su hamsin koh fin haka ," wucewa suka yi tare da nufar sashin da su ka ga ɗazu wasu maza sun bi da buhunhunan abinci . Cikin sanyin jiki suka miƙe tsaye Falmata tana me sake lalubar jikin yakaka wacce ta ke riƙe da ɗayan hannun ta ," Yakaka ya akayi kika faɗi baki ji ciwo ba koh ? Banji ciwo ba falmata ," ku muƙarasa daga can . Watau nan shine masaukin da gwamnati ta tanada domin ɓaki ƴan gudun hijira ,"? Yagana ke furta hakan dai-dai lokacin da suke zama a bakin ɗaya daga cikin fasasshiyar barandar wurin ," a toh ga zahiri dai kin gani ,"cewar yakaka wacce gaba ɗaya ta gama tsinkewa da irin rayuwar da ta hango musu a wannan matattarar kazo na zo ɗin ," Wai yaya fasalin tsarin wajen yake yakaka ?. Yanzu fa ba zama yakamata muyi ba , dacewa yayi mu fara zuwa mu ƙarbi abinci mu ci sai muyi sallah mu bazama neman mama kamar yadda muka tsara ko kuwa ? Haɗa ido yagana da yakaka suka yi kafin yagana ta ce hmmm ai falmata bamu kai ga fahimtar tsarin wajen ba tukun ," ga mu nan dai kara zube kamar yadda muka lura kowa ma a zuɓen yake a wurin nan ," amma bari naje na fara da tambayo mana inda banɗaki yake domin ni mara ta ma cike take dam ," *************** Lalee ,sannun ku jama"a dan Allah ina ne inda banɗaki yake ? Sannan kuma ina ne wurin cin abinci mu ɓaki ne yanzu muka zo ," yagana ke yin dogon bayanin nan bayan da ta tadda wasu gungun mata da su da ƴaƴan su a zaune cikin ɗaya daga cikin ɗakunan nan , Ga mamakin yagana ba wacce ta ɗago kan ta ta ɗube ta bare ma ta sa ran za'a amsa ma ta ," duk kuwa da cewa cikin yaren su tai maganar kuma zanen da yake ɗauke a fuskokin mafi yawan matan wurin da suka kusan tasamma su arba'in ya isa sanar mata cewar daga ƙabila ɗaya suke ita da su ," ɗai ɗaya take kallon su yayin da ta ke jin wani irin ɗan banzan wari da zarnin futsari yana cunƙushe mata kofofin hancin ta ,' ƙudajen da suke yanyame cikin ɗakin da babu koh shimfiɗar tabarma sai ɗaben suminti ," sai kuka suke yuyuyuyu , gami da kukan ƙananun yaran da wasu ma koh ɗan kanfai babu a jikin su , sai tarin layu da zaren jigida a ɗaure a ƙugun su ," shi ya sanya yagana tayi hasashen koh hayaniyar cikin ɗakin ne ya sanya wasu basu ji ta ba ," Sake maimaita bayanin da tayi da farko tayi ," Can baya zaki zagaye kiyi abun da zaki yi maganar abinci kuma ba'a kai ga kammalawa ba ," ki adana sauran tambayoyin ki domin mu ma nan duk da kika ganmu riƙe mu ke da tarin tambayoyin da muke son samun amsoshin su ," Tsam yagana tayi a tsaye bayan da ta gama jin bayanin matar nan ,"jan ƙafafun ta ta soma yi da nufin barin wurin alokacin da taji matar nan ta ɗora da cewa kika ce ku ɓaki ne ? Ke da su wa ? Ba tare da ta jira amsar yagana ba ta ɗora da cewa kun kaima barka domin kuwa a yau gwamna ke kawo ziyara ƙaron farko a sansanin nan ," nan da kika gan mu a zazzaune dakon jiran sa muke ," domin ance tafe yake da tarin kyautukan alkhairi . Ai nan take yagana ta washe baki ji da tayi sun taki sa'a lokaci ɗaya ta ji ta nemi sanyi jiki da taraddadin da ya fara mamaye ta a sakamakon bayanin matar nan na farko ta rasa ," farin cikin albishirin da matar tayi mata na ganin gwamna ra'ayul'ain a yau ya wanke mata bacin ran da take ta shaƙa tun fitowar ta daga garin su ai da gudu ta kwasa har tana murguɗe kafa tayi wurin da ta bar su yakaka . [6/24, 9:58 AM] +234 701 013 7848: Fikrah writers association *MAFARI......* ( _HARGITSIN RAYUWA_ ) *Umm'muaz* 5 Yakaka yakaka ," da sauri yakaka wacce ta maida hankalin ta gaba ɗaya ga mutanen da suke kai kawo a wurin tana nazarin su,"cikin ranta tana hango musu irin rayuwar rashin sakewar da zasu yi ita da ƙanwar ta a cikin waɗannan ɗaruruwan mutanen da basu taɓa sanin koh ɗaya daga cikin su ba ,sanin da tayi su ɗin ba mutane ne waɗan da suka saba da shiga cikin jama'a ba , hasalima su ko a garin su a ƙebe da su da mahaifiyar suke , basa shiga cikin taron jama'a saboda wasu dalilai ," Da sauri ta juya gami da miƙewa tsaye hankali a tashe take duban yagana wacce ta ƙaraso gaban ta yanzu tana ta haki a sakamakon ɗan gudun da tayi ," yagana lafiya ta furta hakan hannun ta ɗaya dafe da kirjin ta ? Lafiya lau yakaka Albishirin ku , ? Da sauri falmata wacce ita ma ta miƙe tsaye ," Da sauri kuma cikin zumiɗi tace goro ? ta zarce da cewa...kin ga maman mu ne ? Ɗan kallon ta da gefen ido yagana tayi cikin ran ta kuwa tausayin su ne ya kawo mata ,! ," Falmata kin manta ni ban san mama ba ?,"ta ɗora da sake faɗaɗa fara'ar ta tace ,"wai yau gwamna ne zai zo wannan sansanin , Yakaka-falmata mu yau mun shigo maiduguri a sa'a ,wallahi yau zamu ga gwamna ta ƙarasa zancen tare da yin ɗan tsallen murna," Ɗan guntun tsaki falmata tayi ,' kana cikin sanyi jiki ta silale tare da lalubar inda ta tashi ta sake zama tare da rafka tagumi hannu bi-biyu , sam a gareta wannan ba Albishir ba ne ," toh ita ina ruwan ta da wani ganin gwamna ? Tukun da wanne idanun zata ga gwamnan ? Sannan koh da tana gani ma a halin da take ciki a yanzu bata jin ganin gwamna zai iya ƙarar da ita wani abu da ya shafi farin ciki da har za'a yi mata albishir a kan sa ,' a halin yanzu jin ɗumin mahaifiyar ta tare da sauraron gwalatun maganar ta ,irin ta kurame shine kaɗai abun da zai sanya ta farin ciki ," hawaye ne ya silalo daga gurbin idanun ta sakamakon amsa kuwwar muryar mahaifiyar ta da taji yana shawagi da yi mata gizo a kunnuwan ta ," Da ɗan guntun murmushi ɗauke akan fuskar yakaka ta koma ta zauna ita ma ," kai yagana saboda haka ne kike ta ihun ƙira na har kika tsinka min zuciya ? Ɗan yaƙe yagana tayi ganin yadda ya da ƙanwar suka gwale ta ," cikin ranta tana cewe ku ai daman alamu sun nuna ba'a yi muku gwaninta Yakaka ni kam ki kaini banɗaki fitsari nake ji kuma fa har yanzu ba mu yi sallar azhar ba har ga shi kamar kunnuwa na suna jiyo kiran sallar la'asar ," Da sauri yakaka ta sake miƙewa lokaci guda tana kai duban ta ga yagana wacce tsabar murna ta gaza tsayuwa guri guda ," yagana inane banɗakin ne ? Ɗan diri-diri yagana tayi domin ita har ga Allah ta ma manta ina aka gwada mata banɗakin yake ,"saboda tsabar ɗoki ," amma ganin wani mutum ya fito daga wani ɗan ɗaki da yake daura da ɗakin da suka fara cin karo da shi a wurin (office ɗin mutumin nan ) hannun sa riƙe da buta ga alama kama ruwa yayi , hakan yasa yagana tayi nuni da wurin ta ɗora da faɗin ,' Kamar cewa aka yi nan baya haka yake koh ,? Bin inda ta nuna da ɗan yatsanta manuniya yakaka tayi ,"cikin shakku take kallon inda yagana ke gwada mata ," domin dai ɗakin da yake gefe da ɗakin (office) ɗin mutumin nan da yayi musu korar kare take nunawa ," Yagana nan baya kika ce kuma gashi kina nuna gaba ? Anya kuwa can ne banɗakin ? Yakaka kina gani dai mutum ya fito daga banɗakin hannun sa riƙe da buta kin dai gan shi ai koh ?," Toh muje falmata ," yakaka ta furta hakan dai-dai lokacin da take kamo hannun falmatan suka jera har bakin barandar ," mu karasa bakin kofar sai na jira ki ," Ɗan turus yakaka tayi lokacin da falmata ta ce toh ina ruwan da zan yi amfani da shi yakaka ? Bari na tambayo matan can inda ake ɗibar ruwa , ta furta hakan lokacin da take mayar da kallon ta kan wasu gungun matan da suke tsaitsaye hannuwan su riƙe da wasu manyan farantai irin na rabawa jama'ar gidan biki abinci , Toh ni zan shiga dan gaskiya a matse nake yakaka idan kin kawo ruwan ki ajiyemin a bakin kofar ," falmata ke furta hakan a lokacin da take laluban ƙyauren kofar ," ɗan bin ta da kallo yakaka tayi cikin ran ta fal tausayi da ƙaunar ƙanwar ta ke ƙaraƙaina ," falmata koh na kama ki mu shiga tare saboda koh banɗakin bashi da kyau sosai ," ? Yakaka zan kula da kaina ki kawo min ruwan da sauri dan Allah kar wasu su shigo kaina ," falmata ta furta hakan a lokacin da ta tura kofar ," Da sassarfa yakaka ta juya ta dumfari matan nan cikin ranta tana jinjina irin karfin zuciyar falmata da kuma yadda a koyaushe take boye tsaraicin ta sosai ,bata taɓa ganin mutum a shekarun falmata da yake da kunya tare da suturce jikin sa irin ta ba ," tun falmata na da kananun shekarun da yakamata a dunga kula da ita irin su wanka ,tsarki da sauran su ," ita bata yadda , sai dai tayi da kan ta duk kuwa da naƙasar da take tare da ita ," tun mahaifiyar su na dukan falmatan idan taƙi yadda tayi mata wanka ," har ta haƙura ta kyale ta . ******** Da lalube take bin bangon banɗakin tana shaƙar wani daddaɗan kamshin da yake game da wurin ,tsam ta tsaya lokacin da ta ji ƙafar ta da koh takalmu babu ta sauka akan wani lallausan abu ,"kamar shimfiɗa ? Da sauri ta ɗan janye ƙafar ta , cikin ranta tana tunanin toh shi banɗakin birni haka yake da laushi kamar anyi shimfiɗa ? Koh da yake ance gidan gwamnati muke ,zata iya yiwuwa ma ayi shimfiɗar a banɗakin dan jin dadi ," Fitsarin da ya sake mintsilin marar ta shi ya sa ba shiri ta ɗan ƙara gaba kaɗan ta sunkuya da nufin tsugunnawa lokacin da taji kan ta yayi karo da wani abun da bata tantance ko menene ba ," ɗan shafa goshin ta tayi lokacin da ta fara sauke larurar ta ,'cikin ranta tana mitar su mutanen birni sai a bar su yanzu me ya kawo tarkace cikin banɗaki ? Ji tayi ana ƙokarin turo kofar da saurin ta tayi gyaran murya cikin siririyar muryar ta tace " a dakata akwai mutum ," Turus yayi sakamakon jin muryar mace da yayi a cikin office ɗin sa ," waiwayawa yayi ya dubi ɗayan saurayin da suke tare da basu wuce sa'o'in juna ba yace ," suleiman ko kaji kamar muryar mutum a cikin office ɗin nan yana dakatar da ni ? ," eh hamza naji mana muryar mace ba ,? "wanda aka kira da suleiman ke furta hakan fuskar sa ɗauke da ɗan siririn murmushin da ya yi kyau akan madaidaiciyar fuskar sa ," Ba tare da jinkiri ba hamza ya murɗa hannun kƴauren gami da danna kan sa ciki" Jikinta babu inda baya rawa a saboda duk ta riga ta gama jin zantukan su , cikin office nake ba banɗaki ba toh inane office ɗin ? kar dai wani wuri ne na musamman wanda bai da alaƙa da banɗaki ni falmata na shiga uku yau ," shine kalaman da suke ta maimaituwa a cikin ranta lokaci guda kuma tana gyara zaman zanin ta da rigar ta har ma da adikon da ke kan ta bayan ta miƙe tsaye ," Ware idanun sa sosai yayi yana kallon ta tamkar dai yaga sabuwar halitta ,tun daga sama har ƙasa , wata irin zabura yayi ya jaa baya sakamakon ganin ruwan da yake kwance male-male akan tattausan shuɗin kafet ( Carpet ) ɗin ofishin daga gefen kafafun ta , tattare fatar goshin sa yayi tare da ƙanƙance idanun sa a lokacin da tunanin sa tare da abun da yake gani suka tabbatar masa da abun da ta aikata masa a office ɗin sa da dazu-ɗazun nan masu shara suka share kowanne lungu da saƙo tare da goge shi haɗi da feshe shi da turare a saboda manyan ɓakin da suke tafe, Da gudu-gudu ta ƙaraso wurin hannun ta rike da zundumemiyar gorar ruwa wacce koh murfi babu , a cike taf da ruwa har yana ɗiga ," ɗan satar kallon saurayin da ta tadda a bakin kofar banɗakin tayi ," da sauri ta ɗauke kan ta sakamakon haɗa idanu da suka yi ta ga yana bin ta da wani kallon da yake nuna alamun kƴamata , Cikin sanyin murya da gurbatatciyar hausar ta tace kayi hakuri yanzu zata fito ɗan ƙwanƙwasa kofar tayi ," falmata ga ruwan kiyi sauri ki fito akwai mai jira ," yakaka ke furta hakan ," Jin ihun fashewar kukan falmata ya sanya ba shiri yakaka ta danna kanta cikin wajen da suke zaton banɗaki ne ," Suman tsaye tayi lokacin da tayi arba da kyakyawan ofishin da yake tashin kamshi ,' hasaso abun da ƙanwar ta ta aikata a ofishin ya sanya ta jin numfashin ta na mata wuyar shaƙa . Muryar sa ta dawo da ita cikin hankalin ta wanda a farko bata lura da wanzuwar sa ba ma a wurin Banza ƴar ƙauye dakikiya , dan ke dabba ce zaki shigo office kiyi min fitsari akan Carpet , ? Ke mahaukaciyar ina ce ? Koh a can ƙauyen ku kin taɓa cin karo da banɗaki da irin wannan tsarin ? Cikin razana yakaka ta maida duban ta ga falmata , ganin ƙanwar ta ɗurkushe dafe da kumatun ta duka biyu ya sanya ba shiri ta saki robar ruwan , nan kuwa take ruwan ya tuntsure ya fara malala a wajen , amma koh ta kan ruwan yakaka bata bi ba ta karasa ga falmata wacce take ta shishiƙar kuka ta ɗago ta tare da rungumo ta baki ɗaya zuwa cikin jikin ta . Falmata meye ya miki ? Dukan ki yayi me ya same ki ? Waɗan nan sune tambayoyin da yakaka take ta faman furta su ga falmata," Ɗagowa tayi tare da falmatan da ta kama jikin rigar yakakan ta maƙalƙale kamar zata koma cikin ta saboda tsabar tsoro da zafin marukan da ta sha , wanda tun da take ba'a taɓa yi mata makamanta su ba ," sai shishiƙar kuka take ta kasa buɗe baki ta bawa yakaka amsoshin tambayoyin da take jero mata, ita burin ta ɗaya kawai su bar cikin wurin da aka kira da offishi ," Da matsanancin bacin rai yakaka ta ɗago idanun ta ta sauke akan fuskar sa wanda yayi kicin-kicin da ita kamar zai kurma ihu hannun sa harɗe a kirjin sa yana ɗosane daga baki-bakin kofar da alama baki ɗaya ma kyamar offishin yake ji a yanzu ," Sauke idanun ta tayi ba domin ta ji raguwar bacin ran da ta tsinci kan ta aciki ba a dalilin fahimtar da tayi ya dokar mata kanwa sai dan wani girma tare da kwarjini da ta ga ya yi mata , gefe ɗaya kuma zuciyar ta na tunasar da ita tare da girmama mata girman laifin da kanwar ta ta aikata da ya sa har wannan gabjejen ƙaton ya mare ta. Ka-kayi hakuri dan Allah bamu sani ba ne , ' shine kalmar da yakaka ta furta a dai-dai lokacin da ƙara taku biyu cikin son ficewa daga offishin , Wani sabon bacin rai ne ya taso masa ganin yadda falmata ta wani ƙwaƙume a jikin yakakan ta ƙi ko da duban sa bare ta bashi hakuri duk kuwa da cewa ita ce mai ɗauke da kaso chasa'in cikin ɗari na girman laifin , Ganin bai motsa ba bare yayi magana ya sa yakaka tayi zaton koh ya haƙura ne ,' dan haka ta saƙalo hannun falmata suka fara taku da shirin barin wajen , sun zo dai-dai ficewa daga offishin Cikin bazata ta ji ya fizgo wuyan rigar falmata ta baya da nan take rigar ta bada sautin ɓarr alamun ɓarkewa , wurgi da ita yayi cikin fitsarin ta faɗa ciki ragwaf , Mahaukaciya waye zaki bar wa aikin goge fitsarin da kika yi min ? Sunkuya maza ki goge shi tas idan ma kuma zuƙewa zaki yi da bakin ki ki maida abun ki inda ya fito ya rage naki , bukata ta kawai kar na ga damshi ," Ke ma kuma ya juya ga yakaka wacce fuskar ta tayi jawur , tare da wani irin mabayyanin bacin rai da har ya sa laɓɓan bakin ta karkarwa , ki sunkuya ki goge ruwan da kika tuttular a nan kafin na kira sojoji su baku horo ,( ya tsora ta su ) Ai kuwa koh dakika ɗaya ba'a ƙara ba falmata ta tattara fiye da rabin zanin ta tare da sanya hannayen ta duk biyu tana laluben daga inda ta fi jin damshin fitsarin ta sanya zanen ta tana guza gurin tare da gogewa da dukkanin ƙarfin ta , idanun ta suna zubar kwallar buguwar da raunin ƙafar ta yayi dalilin wurgi da ita da aka yi , " Da gudu yakaka ta karaso ta sanya hannayen ta biyu ta ɗauke hannun falmatan , " falmata ki bari zaki yaga zanen ki bari na goge ," ba tare da jinkirin kome ba ta warware ɗankwalin kan ta , " tare da sanya guiwar ta a ƙasa ta fara goge wurin ," lokaci guda hawayen da suka taru cikin gurbin idanun ta suka fara sauka , " Yakaka zan iya gogewa nima dai-dai lokacin da ta kai hannun ta tana lalubar jikin yakakan , " zan iya... Sauran kalmomin bakin ta suka maƙale lokacin da hannuwan ta suka sauka akan lallausan yala-yalan gashin ƴar uwar ta, Yakaka ina ɗankwalin ki ? A gaban namiji kike zaune babu rufin kai ? Kwance ɗankwalin kan ta tayi lokaci guda ta rufawa yakakan a bisa kan ta , cikin sauri kuma ta sake tattara bakin zanen ta tare da cigaba da goge kafet ɗin tun karfin ta , Ji yayi idanun sa na son zowa da ruwa , baya raba ɗaya biyu tausayin su ne ya mamaye ransa , sanin da ya yi yana daga cikin mutane masu raunin zuciya ," a hankali ya fara taku har ya ƙaraso cikin office ɗin ,"ba tare da ya dubi fuskar hamza ba ya ce kai ku tashi haka ku tafi abun ku ya isa , nan gaba kuma ku dunga lura da wurare kun ji koh ? Da sauri yakaka take gyaɗa kai lokaci guda kuma ta fara yi masa godiya ," ɗan gyaɗa kan sa yayi idanun sa yana kan fuskar falma da shatin marin da ta sha ya kwanta rudu-rudu . Kamo hannun falmata tayi ta ɗago ta lokaci guda kuma ta zare ɗankwalin falmata daga kan ta tare da rufa mata shi daga kan ta zuwa kafaɗun ta,( da yake ɗankwalin na da girma kaɗan ) Yakaka ke da me zaki rufe kai ? Ba tare da ta jira amsar yakakan ba ta ɗaura hannu da nufin sake cire ɗankwalin ta mayar mata ,"dafe hannun falmata yakakan tayi , idanun ta na cigaba da son taro ƙwalla saboda kumburar da taga fuskar kanwar ta yayi , ba tare da tace kome ba ta dora hannun falmatan bisa kan ta , anan falmatan taji jikakken ɗankwalin da yakaka ta ɗaura akan ta wanda ta goge wurin nan da shi ," da sauri falmata ta buɗe baki da niyyar sake cewa wani abun ," katse ta yakaka tayi cikin cewa mu tafi falmata ," Taku suka fara yi hannayen su saƙale da na juna ," sun zo dai-dai kofar yakaka ta maida duban ta , kan sa sarƙewa idanun su yayi cikin na juna ," kallon-kallo suka yi na ƴan dakiƙai ,'kowannen su zuciyar sa na bugawa da yanayin da take ciki , " A bangaren sa haushin su duka biyun ne fal a ran sa! Tare kuma da jin takaicin me ya sa suleiman bai bar shi ya hora waɗan nan gidadawan ba son ran sa ta yadda gaba baza su sake gigin yin ganganci makamancin wanda suka yi a yanzu ba , yayin da wani bangare me rangwamen rinjaye yake jin wani abu me kama da bai fa kyauta ba , musamman a yanzu da ya kalli cikin ƙwarar idanun ta masu ruwan zaiba-zaiba ,sai ya ji wannan yanayin kamar yana sake ƙarfafa acikin ran sa ,! Tsaki ya jaa a lokaci guda yana mai kau da kan sa , Ga yakaka kuwa ,' lokacin da take kallon ƙwarar idanun sa baƙar shaida take yi masa tare da jin tsanar sa tana mamaye baki ɗayan zuciyar ta tana jin shine mutum na farko da ta fara tsana a cikin rayuwar ta , sakamakon rashin tausayi ƙarara da ya nuna a gare su uwa uba , shi ɗin ne mutum na farko da ya taɓa lafiyar ƙanwar ta abar ƙaunar ta akan kuskuren da ta aikata shi cikin rashin sani ,ba tare da ya dubi naƙasar da ke tare da ita ba ," ɗauke kan ta tayi lokacin da suke sanya kafafun su domin barin ofishin , Baku ji ba ," waiwayowa yakaka tayi lokaci guda tana me jin faɗuwar gaba ," a hankali ya ƙaraso hannun sa a aljihu , zare hannun sa yayi daga aljihun ya fiddo da sabuwar naira dubu ɗaya ," ungo ku sayi hijabi ku dunga sanyawa ," ganin basu ƙarba ba ya sanya yayi ƙasa da hannun sa dai-dai hannun falmata ya taɓa hannun nata da kuɗin cikin buɗe muryar sa yace ," Ƙarbi mana ,' duk da cewa falmatan ba gani take ba hakan bai hana ta juya fuskar ta inda take jin hucin numfashin yakaka ba ," da alamun neman izni bisa fuskar ta ," Mungode Allah ya saka da Alkhairi amma baza mu karbi kuɗin ka ba a wurin Allah muke neman taimako ta hannun gwamnati muna tunanin gwamnati ke da Alhakin ɗaukar nawin mu ,? Dan haka baza mu ƙarbi kudin ka ba mun gode sosai ," cewar yakaka daga haka ta jaa hannun falmata suka ƙarasa barin wajen. Ɗan murmushi suleiman yayi lokacin da yake bin bayan su da kallo , lokaci guda yana jin tausayin su yana ratsa shi , gefe guda na ran shi ji yayi kyakyawar tarbiyyar da ya ga alamun ta a tare da su ta burge shi , juyawar sa yayi bayan ya maida kuɗin sa aljihu ," Amma wallahi hamza baka kyautawa a wasu lokutan ,abun da kayi ga waɗan nan yaran sam bai kamata ba , baka ganin ƙauyawa ne ? Ya kamata ka dunga rage zafin zuciya tare da tausayawa na ƙasa da kai Dan Allah . Mts toh uba na idan ka gama min faɗan sai ka fita ka samo Cleaner ya zo ya goge wurin tun da ka sallami masu ɗauke da alhakin gyaran kaji koh waliyyin Allah ? Yakaka , Falmata wanka kuka yi ne naga jikin ku du a jiƙe haka ? Falmata meya ya same ki haka fuskar ki a kumbure faɗuwa kika yi a banɗakin ? Ganin sun wuce basu tanka mata ba ya sa yagana bin bayan su tana me sake ƙare musu kallo daga sama har ƙasa ," a ranta kuwa ta fara jin haushin irin halayyar da suke gwada mata a wasu lokutan ,' musamman ma dai falmata , Yagana meyasa kike yin ƙarya ? Tun muna yara maman mu ta nusar da mu rashin kyaun faɗar zancen da ba gaskiya ba ,meyasa kika ce mana can wurin banɗaki ne alhalin kin san ba haka bane ? Dubi jikina dubi jikin falmata kuma ki dubi fuskar ta ? Duk sanadin kin faɗa mana zancen da ba gaskiya bane kika jawo mana wannan masifar ya zaki ji idan mu ne muka tura ki cikin haɗari irin haka ,? Cikin nadama yagana take kallon fuskar yakaka wacce take bayyana tsantsar bacin rai a lokacin da take sanya sauran guntun ruwan da ta ɗibo tana wankewa falmata jikin zanin ta ," Kuyi hakuri yakaka na ɗauka banɗaki ne ganin wani mutum ya fito daga ɗakin yana gyara wondon sa da buta riƙe a hannun sa , A fusace falmata ta katse ta wacce ta zo har wuya da bacin ran yagana domin ita ce ainahin sanadin faruwar kome ," amma ai yagana cewa kika da farko an gwada miki can wurin ne banɗakin ? Meyasa kike haka tun farkon fara tafiyar mu tare zantukan ki dayawa ba gaskiƴa kike faɗa ba, haka kika ce mana kin san hanyar maiduguri ? Ba domin Allah ya haɗa mu da mutanen dajin nan ba(fulanin da suka taimake su ) da ba mu san halin da zamu shiga ba ," yagana yana da kyau mutum ya dunga faɗin gaskiya kome wuyan ta . Cikin takaici yagana take kallon falmata wacce take daga zaune idanun ta suna kallon gefe ," tayaya za'a yi ƴar karamar yarinyar da ta girmewa , ta zauna tana gaya mata magana son ran ta ? Tana yi mata tsawa da ihu irin haka kuma ƙarin abun takaicin ma makauniya ce miskiniya ," Dakata falmata daga yau sai yau ni ba sa'ar ki bace dan haka kar ki sake cewa zaki min faɗa da tsawa ," meyasa ku da kuka shiga wajen kuka ga ba banɗakin bane ba ku fito ba ,? Koh kuwa ba tare muka zo wurin ba ɗazun nan ? Da dan kawai nayi kuskure zaku hau kaina da faɗa yayar ki tana min ke ma kuma kice zaki min kamar ku kuka kawo ni garin ? Cikin sanyin jiki yakaka ta bi bayan yagana da kallo wacce bayan ta gama mayar musu da magana ta kaɗa kan ta ta bar wajen ba tare da ta sake ce musu ƙala ba , ta koma nesa da su ta zauna , alamu sun nuna taji haushin faɗa mata laifin ta da suka yi , Wanda ita kuma yakaka sam hakan bai mata daɗi ko babu kome cikin kwanaki biyun da suka yi tare da yagana taji daɗin samun ta a matsayin ƙawar da suka shigo sabuwar rayuwar su a tare , kuma ƙwarai yagana tana kokari wurin kyautata musu musamman ma dai falmata ," toh sai dai har ga Allah ita bata son hallayar da ta lura yagana ta na da ita na ƙarya , ba dan kome tayi mata magana ba sai dan tana son yagana ta bar hallayar dan ba hallaya bace mai kyau , duk da haka cikin ran ta ta ƙudurci aniyar bata hakuri tun da ta ga tayi fushi, sam ita baza ta so rabuwar su ba ,ƙwarai take bukatar ƙawa cikin rayuwar ta a yanzu wanda a tun tashin ta bata damu da ƙawaye ba , falmata ita ce ƙawar ta abokiyar wasan ta , amma a yanzu da girma ya hau kan ta ya zama dole ta nemi wata ƙawar bayan falmata da zata dunga taya ta koh da da shawarwari ne domin inganta rayuwar falmatan . ƙamshin abincin ne ya daki hancin su da ya sa ba shiri yakaka ta bi manyan farantan da aka wuce da su da kallo nan take yawun bakin ta ya tsinke ganin shinkafar da aka wadata kan ta da baƙar miyar da tashin farko ba za'a tantance jar miya ce koh kuwa wacce irin miya bace , amma da yake cikin su ya jima rabon sa da abinci sai abincin yayi kyau matuƙa a idon yakaka ," Yakaka ƙamshin abinci nake ji ? Muje mu ci mana koh ba namu bane ? Falmata ta ƙarasa zance tare da haɗiyar yawun da kamshin abincin nan ya sanya shi tsinkewa ," Wucewa aka yi da abincin inaga rabawa ake dan naga gashi sai kaiwa ake wuri-wuri ," inaga mu ɗan jira za'a zo kan mu ," Miƙewa tsaye yagana tayi tare da ƙarasawa bakin kofar ɗakin da ɗazu ta shiga tayi tambaya wanda yanzu ta ga an shiga da farantan abinci huɗu ," Dogarewa tayi daga bakin ƙofar tana ganin yadda matan nan kusan su arba'in da ƴaƴan su ,suka tasamman farantan abincin nan huɗu haiƙan da suke tashin tiririn zafi . Hannu baka hannun ƙwarya suke auna abincin nan zuwa cikin bakunan su yayin da ƴaƴan su waɗan da wasun su basu wuce ƴan shekaru biyu ba zuwa ƙasa , su ma ba'a bar su a baya ba, kokawa suke da tiren abincin nan wasun su hannu bi-biyu suke jefawa cikin tiren basa koh nuna alamun jin zafin abincin , na bakin su yana komawa ciki sakamakon ƙona musu harcen da abincin ya ke , Cikin mintocin da suke ƙasa da biyar babu abincin nan babu alamun sa tamkar dai gonar hatsin da mayunwatan tsuntsaye suka sauka a kai suka tashi , haka kan farantan nan suke babu koh ƙwarar shinkafa ɗai , sai tashin tiririn da har yanzu da suka kammala cin abincin bai kai ga hucewa ba , ƴaƴan su suna ta sanya harce suna tanɗar jikin faranti tamkar zasu haɗa da farantin su lanƙwame . Sauke ajiyar zuci yagana tayi lokacin da suka haɗa ido huɗu da matar da ta yi mata kwatancen banɗaki a ɗazu "tana ta faman tanɗar yatsun hannun ta lungu da sako tana zura harshe tana zaƙulo duk wata guntuwar miyar da ta rage mata a hannu ," yarinya ke ba anan za ki ci abinci ba ki tafi ta can bayan tantunan da suke farfajiya anan ƴan mata sa'o'in ki suke kiyi sauri ki tafi kar a cinye a bar ki , cewar matar nan da yanzu ta kammala suɗe hannun nata ta goge hannun akan ta . Ba tare da tace kome ba ta juya gami da kai hangen ta ga harabar wajen can ta hango masu rabon abincin nan sun nufi manyan tantuna biyun da suke haɗe da junan su daga gefe ," da sauri ta ɗiro daga kan dakalin barandar har ta ɗaga kafafun tayi taku biyu sai ta waiwaya karaf suka haɗa idanu da yakaka wacce duk ta bi ta damu da fushin yagana , hakan ya sa duk wani motsin yaganan yake kan idanun ta ," Yafitar su tayi da hannu lokaci guda ta buɗe murya ", Yakaka ku zo mu je mu ci abinci a can ," ba tare da ta jira amsar su ba ta ɗaga ƙafafun ta cikin sauri ta nufi tantin da ta ga an kai abincin nan cikin ran ta cike da addu'ar Allah ya sa ba'a riga an fara ci ba . Da sauri ta ruƙo hannun falmata da jin zancen abincin nan ya sa cikin ta ya sake yin ƙarar yunwa , Mu yi sauri mu je falmata ! [6/24, 9:58 AM] +234 701 013 7848: Fikrah writers association *MAFARI......* ( _Hargitsin rayuwa_ ) *umm'muaz* 6 Jugum suka yi a ɗosane tsakankanin matsin ƴan mata sa'o'in su da waɗanda suka fi su , da ma ƙasa da shekarun falmata kaɗan "bayan kammala baɗakalar wawason abincin,. Yakaka ni fa koh rabin-rabin yunwar da nake ji bata mutu ba ,wannan abincin sam bai isa ga uwar hanji na ba , me zai hana mu nemi wurin sayar da abinci mu sayi wani da kuɗin hannun mu ? Kiyi hakuri falmata mu jira na dare tun da kin ga yanzu la'asar yayi ,idan yaso da daren sai mu shirya salon cin abinci , tun da kin ga dai yadda muka sha gumurzun kokuwa kafin mu samu ƴan lomomin da yanzu suke cikin mu . Toh yakaka ,Allah ya kaimu ɗaren . Cikin wani irin yanayi na tausayawa yagana take kallon yakaka wacce koh lomar abinci ɗaya bata sa cikin bakin ta ba , domin duk kokuwar da ta sha idan ta ɗebo abincin maimakon ta sanya a bakin ta , lalubar hannun ƙanwar ta take ta zuba mata , Cikin neman son su shirya bayan ƴar hatsaniyar da ta shiga tsakanin su ,"yakaka ta sakarwa yagana murmushi tare da riƙo hannun ta , mun gode yagana ba domin kin kira mu ba ,"da baza mu samu abincin ba" Murmushi yagana ta mayar mata ,"babu kome yakaka mun riga mun zama ƴan uwa " Waiwayawa tayi ga wata budurwar da take zaune kusa da ita "ta ɗuƙufa sosai wurin soka allura da zarewa a jikin hular da take ɗinkawa ", Dan Allah kawata koh zaki gwada mana banɗaki muna so muyi sallah? Cewar yagana Ba tare da ta ɗago daga yin ɗinkin da take ba tace ,idan kuka fita kuyi hannun ku na dama ku miƙe sosai zaku tarar da banɗaki a jere amma ku kula hudu daga cikin takwas ɗin basu da kyau duk sun tsage sun farfashe ba'a amfani da su dan gudun su rufta da mutum . Godiya sosai suka yi mata dai-dai lokacin da suke miƙewa . Da ido yakaka take bin farfajiyar da take dauke da banɗakunan da kallo cikin wani irin yanayi na tsantsar kyankami domin duk da kasancewar su mutanen ƙauye ," suna da wadatar tsafta basa barin muhallin su cikin dagwalon ƙazanta ," Cikin ɗaukewar numfashi falmata tace kai yakaka wannan banɗaki da wari yake da alama babu wadatuwar tsafta , ni dai gwada min inda zan yi alwalar . Koh kafin ta buɗe baki "yagana ta karaso wurin hannun ta riƙe da manyan gorar ruwan roba wanda mafi akasarin mutanen wurin suke amfani da ita a madadin buta . Itama turus tayi ganin tsimi-tsimin "bahaya" a farfajiyar wurin wasu an turbuɗe da ƙasa wasu kuwa muraran suke a sarari ƙudaje tare da sauran ƙwari suna sukuwa a kai . Da sauri ta kawar da kai tare da tsirtar da wani mugun yawun da taji ya taru mata a baki tace ,"yakaka anya wurin nan kuwa ya dace da wajen alwala ? Gaskiya ku zo mu koma Bata gama rufe baki ba ,"taga wata mata da goyon ƴar ta,  ta zo tayi ƴar tsallaƙe ta tsallake tarin kazantar dake wurin tare da shiga ɗaya daga cikin banɗakin wajen ,"cikin ƴan dakikai kuma wata mace ta fito daga ɗayan banɗakin . Yagana babu yadda zamu yi kin ga kowa dake nan wurin da nan ɗin suke amfani , dan haka muma dole mu bi ayari . Tana rufe baki ta saki hannun falmata gami da tattare zanen ta , ta tsallaƙa cikin dauke numfashi ta nufi bandakin ,"tare da cewa falmata ki jira ni anan kar ki motsa ", Bayan sun idar da sallolin da ke kan su da suka yi ta a ɗanɗaryar ƙasar kan baranda ,cikin rashin wadatuwar suturar da zasu suturce jikin su kamar yadda ya kamata a yayin sallar ," duk da daman ba wani sani suke da shi sosai game da ibadar ba . Tsumu suka yi kowaccen su cikin taɗin zuci ," Ƙarar jiniya da tayi musu kama da ta motar sojojin nan da suka ji ya dumfaro farfajiyar masaukin nasu ,shi ya firgitar da su suka miƙe ba shiri cikin ransu kuwa cike da taraddadin da me jiniyar ta sake zuwa musu a karo na biyu cikin ƙasa da sa'o'in su biyar a cikin birnin na maiduguri ? Sai dai sabanin tunanin su a yanzu ba daga motar sojojin da suke zato bane ƙarar jiniyar take fitowa ba ," daga wasu jerun gwanon manyan bakaƙen motoci masu daukar ido tare da kyallin sabuntar dake nuni da tsadar su , karar take fitowa ", Buɗe baki da hanci yakaka,da yagana suka yi suna bin motocin da kallo waɗanda har matukan su suka riga suka sama masu matsaya ," Sai dai basu kai ga sauke numfashin farin cikin da suka riƙe na ganin cewa ba waɗannan sojojin da ganin su ba alheri bane a wurin su ,suka dawo ba , idanun su suka yi arangama da jerin gwanon motocin sojojin daga baya da ma na wasu jami'an tsaron masu mabanbantan kayan sawa wadanda basu kai ga rarrabewa da banbancin su da sojojin ba  ," Mukut ! Yakaka ta haɗiye yawun tsoron da ya cika mata zuciya fal ! Lalubar hannun ta falmata tayi cikin maƙyarkyatar murya take cewa " yakaka, yagana kun ga abun da nake faɗa muku koh ? Ni daman nasan da kyar idan ba gidan bayar da horo sojojin nan suka kawo mu ba ," ai tun daga horon yunwar da aka fara yi mana ɗazu ya ci ace kun fahimci irin kurkukun da muka shigo ," kawai ban faɗa miki bane yakaka , amma tun sanya kafafuna cikin garin maiduguri naji ajikina babu alheri cikin sa , naji cewa akwai wani babban al'amari marar daɗi da zai same mu a cikin sa ," Kuwwar mutane tare da dararrakin su da ya cika musu kunnuwa shi ya katse surutun da falmata take yi cikin ɗimaucewa ta koma cewa "menene yakaka ? Harbi ake ? Kashe mu muma zasu yi ? Toh ku zo mu gudu mana tsayuwar me muke ? Ki nutsu falmata ! Yagana ta furta "cikin ɗan ɗaga murya" a sakamakon surutun da hargowar da falmatan take yi musu cikin ruɗewa ya hana ta , ta gano abun da take hasashe , ganin yadda taga fuskokin kowa a wurin ya yalwatu da fara ,"ta ko'ina bullowa jama'a suke suna tururuwa a harabar wajen ," Da gudu yagana ta dira daga kan baranda kafin ta waiwayo cikin tsantsar farin cikin da kamar anyi mata babban bisharara ,"yakaka falmata ga gwamna wallahi gwamna ne yazo ,gwamnan jahar borno ", kuyi sauri ku taho kar wajen tsayuwa ya cika ," daga haka ta kara da gudu kamar yadda taga sauran jama'a maza da mata suna kwasar gudun zuwa gaban dandamalin da jami'an tsaro suka kewaye ta ko'ina wanda da alama anan gwamnan yake tsaye . Saƙare suka yi a tsaye  cikin rashin sanin takamaimai halin da suke ciki na farin ciki koh saɓanin hakan , a zahiri basa jin wani farin ciki a dan saboda zuwan gwamnan musamman ma ga falmata ," wacce ta sauke boyayyar ajiyar zuciyar samun kwanciyar hankali jin ba zuwa aka yi domin azabtar da su ba kamar yadda ta zata ," sai dai ita bata wani farin ciki da zuwan gwamnan domin rashin sanin muhimmancin zuwan nasa . A hankali yakaka ta fara jaan hannun falmata cikin cewa mu ma muje falmata muga gwamnan kuma muji bayanin sa kin ga duk mutane sun tafi . Bayan gajeren bayanin da gwamnan ya gabatar musu cikin yaren su wanda duk na ban hakuri ne game da halin da suke ciki tare da yi musu alkawurwukan kyautata musu da ababen more rayuwa , sannan a karshe yayi musu albishirin tarin kayan abinci da suke tafe da shi , gidajen sauro , butoci da kuma bargunan rufuwa , ya kuma ƙara da albishirin za'a ƙara musu matakan kula da lafiyar su da sauran bukatun su na yau da kullum, a karshe kuma ya basu dama wasu daga cikin su suka faɗi irin matsalolin da suke ciki a sansanin nasu , inda mafi yawan korafe-korafen nasu ya tafi akan ƙarancin abinci da ruwan shaa,  uwa uba da cizon da sauro da ƙwarin gurin suke musu wanda cizon sauron yake kawo musu mummunar masassarar da har take iya kaiwa ga rasa rayuka idan ya zo da ajali musamman ga mata masu ciki da kananan yara . Bankwana yayi musu bayan da ya basu tabbacin za'a samu sauyi daga yanzu inda ya nemi da a naɗa kwamiti da shuwagabanni a tsakanin su kashi-kashi domin lura da matsalolin su . Nan take aka shiga ihu da kalmomin yabo ga gwamna da tawagar sa har zuwa lokacin da ƙurar motocin su suka bace . Babu laifi , ziyartar da gwamna ya kawo musu sosai ta saisaita ciwukan da suke cikin rayukan al'ummar sansanin yayin da ya haifar da farin ciki a cikin zukatan kashi tamanin na cikin ɗarin mutanen. Idan aka ɗauke falmata wacce har kawo yanzu da ake kammala raba musu gidajen sauro tare da barguna, inda ake haɗa mutum biyu da gidan sauro guda bayan an damƙa musu bargunan su ɗai-ɗaya da buta ɗaya ," dukkanin su ba'a haɗa su da juna ba ,an ware su ne daban-daban yayin da aka haɗa yagana da wannan budurwar wacce ta basu kwatancen inda banɗaki yake , yakaka kuwa da wata yarinyar mace mai yara biyu ƙanana aka haɗa ta , falmata kuma da wata mata wacce take yanayi da zaurawa ,"domin ta wuce a sata sawun ƴan mata ƙanana irin su ,"kuma ita bata da ɗa ," babbar budurwa dai . Babu yadda yakaka bata yi da wannan babbar budurwa da aka haɗa su da falmata akan tayi musu lamini ta bar musu ita da falmata gidan sauron idan ya so sai itama yakaka ta bar mata wajen ta ,"ma'ana suyi musanye wuri," saboda a zahiri ta shiga tashin hankali ganin za'a raba musu wurin kwana da ƙanwar ta ," Amma fir budurwar nan taƙi ,tace ita gaskiya baza ta iya kwana cikin gidan sauro guda tare da mai yara ba , karshe ma ta fatattaki yakaka ta kuma ce idan har ta matsa toh fa sai dai falmatan ta bita su tafi chan su ƙarata "ta bar mata gidan sauron ita ɗaya " Da farko yakaka tayi tunanin su haƙura kawai da kwanan cikin gidan sauron su haɗu su dunga kwanan su tare, sai dai tunowa da korafe korafen da taji ɗazu sun yi da suke faɗin illar da cizon sauron yake yi da har yake iya kisa , yasa taji babu yadda zasu yi dole ta kiyaye lafiyar falmata , dan haka tana ji tana gani aka raba musu wurin kwana da ɗaki ita da ƙanwar ta . Dare ya raba tsakiya idan banda juyi babu abun da falmata take yi gaba daya ta kasa bacci saboda tsananin takurar ta da budurwar da ake kira da "ajus" taƴi duk ta bi ta ture ta, tare da janye mata bargonta ta rufu da shi ,sakamakon sanyin damina tare da raɓa irin na tsakiyar daren yanayin damina ," sakamakon turo ta da ta dunga yi yasa gidan sauron nasu duk ya buɗe sauro da cinnaku masu fiffike sun samu damar shiga ciki sai faman ɗallara mata cizo suke ,"sau biyu tana yunƙurin jaan bargon ta amma sai ajus ta ɗallara mata mintsini tare da haure ta da ƙafa ," Lalubawa tayi ta tashi ta zauna tayi tsumu , gefe ɗaya na zuciyar ta cike taf ! da kewar mahaifan ta da ƴan uwan ta ,"kamar yadda take sake ganin daren na yau ma kamar sauran ukun da suka wuce babu mahaifiyar ta babu mahaifin ta babu ƙannen ta ," duk wani buri da take da shi na samun gamuwa da mahaifiyar ta da sauran ƴan uwan ta taji yana barin ran ta , wani sashi na ranta yana raɗa mata tare da bata tabbacin sun rabu kenan har abada," fashewa tayi da kuka dai-dai lokacin da wata gwarzuwar cinnaka ta sake mallara mata cizo a dokin wuya ,"cikin zubar hawaye take tuno irin kulawar da mahaifiyar su ke basu a irin wannan yanayin na yawaitar muggan kananan kwarin damina sam bata bari su cutar da su ,"toshe kunnuwan ta tayi da hannayen ta biyu a sakamakon rugugin hadarin da taji wanda take da tabbacin ruwan sama gaf yake da tsinkewa A hankali yakaka ta sauke ɗan jaririn mai kimanin watanni biyu zuwa uku daga kan kafaɗun ta a yadda take durƙushe cikin gidan sauron tana ta faman jijjiga shi ,"tayi niyyar kwantar da shi a gaban uwar sa wacce take bararraje , tayi wawiyar kwanciya cinyoyi duk a buɗe kai ba ɗankwali ," cikin addu'ar Allah yasa kar ya farka domin hakika ta gaji da rainon sa tun farkon dare yake hannun ta lokacin da uwar sa ta dungura mata shi tace ta jijjiga shi yayi bacci,  ita ta gaji bacci take ji ,ta jaa ɗayan ɗan nata gaban ta suke shaƙar baccin su ,"sau uku tana ajiye shi amma daga yaji an ajiye shi baya yin minti ɗaya yake sake challara kuka ," cikin gigin bacci da hargowa uwar sa zata ce dallah ta ɗauke sa zai hana sauran mutane bacci . Cikin sa'a har ta kwantar da shi bai tashi ba ," tsurawa kofar ɗakin ido tayi tana ganin yadda walƙiya take haskawa tare da rugugin hadari nan take hankalin ta ya tashi tunowa da falmata da tayi koh a wane hali take ciki a ɗakin da take ? Ji tayi baza ta iya kwanciya ba idan bata ganta ba . A hankali ta ɗaga gidan sauron da suke ciki da niyyar fita dai-dai lokacin da aka yi wani tsawa da rugugin tasowar hadari da ya sa jaririn nan ya firgice tare da tsanyara kuka ," a daburce uwar sa ta farka gami da fara cewa ke ke keh kina ina ne kika bar shi yana ta irin wannan ihun ji min ƴar banzar yarinya ,"muguwa ,cikin sanyin murya yakaka tace wallahi yanzu na ajiye shi koh kwanciya ban kai ga yi ba , kuma ma da alama kamar yunwa yake ji ", ta furta hakan cikin fatan Allah yasa uwar ta ɗauke shi ,"mts ta jaa tsaki tare da surar ɗan jaririn kamar ta suri yaro mai shekaru biyu ," ta koma ta kwanta tare da shi tare da ciro abincin sa ta cusa mar a baki ,ɗif yayi shiru . Sauke ajiyar zuci yakaka tayi ganin uwar da ɗan sun koma bacci ,"ta siɗaɗa ta fita dai-dai lokacin da kakkarfan ruwan saman ya tsinke kamar da bakin ƙwarya ," gudu-gudu ta tsallaka ɗayan barandar ɗakin da falmata take ,'ba tare da ta damu da duhu tare da shirun da harabar wajen ya ɗauka ba ,ga ƙarar ruwan sama ," Tana shiga ta fara yawata idanun ta ," a hankali ta fara jin ƴar siririyar muryar ta tana kuka ,"ɗas-ɗas zuciyar ta ta buga tare da taruwar ƙwalla cikin gurbin idon ta,  cikin sauri ta fara taku tana kewaye gidajen sauron jama'ah tare da tsallaƙe su cikin taka tsantsan ," tana nufar inda take jin sautin ta domin bata son yin magana kar ta tashi mutane Cak ta tsaya da kukan jin takun sawayen ƴar uwar ta ,"yakaka ta furta cikin sanyin murya dai-dai lokacin da ta ƙaraso tare da durƙusawa a bakin "shingen"(gidan sauro) . Ƙasa-ƙasa tace falmata meye yasa ki kuka ? Me aka miki ," da shishiƙar kuka tace babu kome yakaka na tuno da su mama ne ,"yakaka cikin daren nan kika fito kuma ana ruwan sama ? Meyasa ?  ki koma ki kwanta dan Allah cikin ƙura ido tare da taimakon hasken walkiya ta fahimci a dandaryar ƙasa kanwar ta take takure a zaune ," cikin takaici ta maida duban ta ga ajus da take ajiye numfashi ɗaya bayan ɗaya tare da sake duƙunƙunewa cikin jin daɗin barcin ta ,take ta fahimci abun da yake faruwa ," Zuruf ta miƙe cikin cewa ina zuwa falmata ," bata saurari amsar falmatan ba ta fita , Jim kaɗan ta dawo tare da bargon ta a hannun ta zura hannu  ta miƙawa falmatan bargon,"ungo falmata buɗa shi ki kwanta akan rabi ki rufu da rabin duk da ma dai fitsarin yaron matar chan ya taɓa jiki amma ki kwanta a haka ," Jin falmatan tayi shiru yasa tace matsa na shinfiɗa miki kin ji ,"? Cikin rawar murya tace yakaka ke kuma ki koma ki kwanta akan me ? Shittt ," falmata lafiyar ki tafi min kome , bamu da kowa a yanzu daga Allah sai junan mu , menene amfani na idan har ban zamar miki garkuwa ba falmata ,"  tana furta hakan ne dai-dai lokacin da take gyara mata bargon tana shimfiɗa mata ," kama mata tayi ta kwanta ," Yauwa toh bari ruwan ya ɗan tsagaita sai na koma ɗakin mu kiyi baccin ki kin ji ? Gyaɗa mata kai tayi domin kuwa idanun ta har yaji-yaji suke mata tsabar baccin da ya cika su , Sauke sassanyan numfashi tayi , tare da share guntun hawayen da ya cika mata gurbin ido nisawa tayi tana tunanin ƙalubalen da suke a farkon sa yanzu wanda basu da sani akan iyakar sa ,karshen sa babu abun da yafi tsaya mata a zuci irin tausayin ƙanwar ta a yin rayuwa cikin wannan sansanin da ta lura kowa kan sa ya sani kan sa yake so "rayuwar daga ƙawri sai gwaiwa ",  zuciyoyin mutane cike take da mugunta da son kai .. Yaa Allah ga ni ga miskiniyar kanwata Allah ka taimake mu .                *Maraɗi jamhuriyar niger*  A karo na biyar ta kama ta sauko daga kan murfin sunduƙin yin "bahaya"( Toilet- Toilette ) da yake cikin banɗakin ta ," kai kawo ta shiga yi tare da duban agogon fuskar wayar ta " Yau har karfe biyu da mintuna arba'in biyamuradi bai dawo ba kamar yadda ya saba fita sha biyu da rabi na dare ya kuma dawo karfe biyun dare ," Meye ya tsayar da shi ? Jin motsi tayi kamar an taɓa kofar sirrin da take bangaren biyamuradin wacce kuma da ita yake amfani wurin fita da shigar sa gidan a dai-dai wannan lokutan da ba wanda ya taɓa sanin yana fita daga Allah sai shi sai ita ,  Cikin sauri ta sake ɗarewa kan sunduƙin tayi ƴar ɗage ta leƙa ta ɗan siririn huɗar da aka yi ta a can saman banɗakin domin ado wanda aka liƙa kwan lantarki a jiki, sai dai a halin yanzu babu ƙwan lantarkin sai dai huɗar da ta fito sarari ake iya ganin abun da ke waje ta wurin , Tar ta hango shi a cikin hasken lantarkin da ya ƙawata lambun bayan ɗakunan sa ," yana layi tare da tamɓele jikin farar rigar sa da shuɗin wandon jins ɗin sa dumu-dumu da abun da bata iya tantance shi daga inda take ," Ji tayi ruwan hawaye ya silmiyo daga gurbin idanun ta da gudu sun fara tsere akan siriryar fuskar ta ," Wani faɗuwar ƴan bori da yayi rigijib shi yasa ta kusa zamewa ta silmiyo daga kan toilet ɗin ,  da sauri ta ɗiro cikin gudu-gudu ta bullo ɗakin ta tare da fitowa cikin parlour kai tsaye ta nufi kofa ta kama mariƙin kofar ta murɗa , zuciyar ta tana zafi tare da ingiza ta , idanun ta suna hango mata faɗuwar da abun kaunar ta yayi . Sai dai turus ta jaa ta tsaya lokacin ta tuno da fitar ta a wannan lokacin zuwa bangaren biyamuradi zai jawo , me zata cewa masu tsaron gidan ? Wanda ta san basu san halin da yake ciki ba , basu taba sani ba , idan kuwa har ta fita war haka dole su sani . Hakan yana nufin fallasuwar mummunar fuskar masoyin ta , hakan yana nufin kunyatar masoyin ta , hakan yana nufin dasuwar bakin ciki cikin zuciyar uwar goyon ta , hakan yana nufin samar da wanzazjen bakin ciki cikin zuciyar uban goyon ta kuma kawun ta , hakan yana nufin tozartuwar ƴan uwan ta ,hakan kuma yana dai-dai da zubewar girma da mutuncin masarautar su baki ɗaya . Kamar walƙiya ta juya ta koma da sassarfa ta shiga ɗakin ta gami da murza mukulli lokaci guda ta nufi gadon ta gami da fadawa rubda ciki ta sanya kanta tsakanin filo gami da fashewa da wani irin kukan da ya tuƙo tun daga karkashin zuciyar ta , kuka ne irin wanda mutum yake yi idan bakin ciki yayi masa yawa . *Sorry this is a really short chapter koh? Kar ku damu insha Allah the next one will be longer and more action packed !* *Things are really starting to heat up now* 😜 *Please comment what you guys think of not just this chapter but every chapter . I really love hearing feedback on my work because these chapters are not easy to write .* *#Thanks* . *#son so* *#mafari Yanzu muka fara* [6/24, 9:58 AM] +234 701 013 7848: Fikrah writers association *MAFARI.......* ( _Hargitsin Rayuwa )_ *umm'muaz* 7 Juyi ya sake yi a karo na barkatai bisa makeken gadon nasa na alfarma, tare da runtse idanu yana mai sake jin yadda kan sa yayi masa mugun nawi har baya iya buɗe idanun sa sosai , ɗan ƙaramin tsaki ya jaa da yayi sanadin juyowar Tafeedah wanda yake zaune bisa doguwar ƙawatatciyar kujerar da take gaba ƙadan da gadon . Cikin takaici yake duban biyamuradi yousouf ɗin , kafin ya ɗan yi gyaran murya ! "cikin kowanne daƙiƙa ɗaya da yake wucewa yana sake nisanta ka da lokacin sauke farillah " tafeedan ya furta kalmomin masu nuni da tunasarwa , cikin nuna halin ko in kula ga biyamuradi yousouf , wanda koh kafin tafeedah ya idasa bayanin sa ya buɗe idanun sa tarwai da jijiyoyin cikin suka yi jaa , kammala bayanin nasa ya zo dai-dai da miƙewar sa zumbur daga kan gadon . Bai yi wani jinkiri ba ya fara taku cikin sassarfa lokaci ɗaya yana sauke idanun sa akan tagar ɗakin sa wanda hasken rana ya riga ya hudo ta tsakanin labulen . Bayan tsawon mintoci fiye da talatin da biyamuradi youssouf ya ɗauka yana addu'a da neman gafarar mahaliccin sa bayan ya idar da sallah , sadda kansa ƙasa yayi yana me jin kunyar ɗago kansa ya dubi aminin nasa wanda ya tabbatar idanun sa a kafe suke a kan sa , yayin da sashi guda na zuciyar sa yana me son tuno da wani abu . A firgice ya dago kan sa a sakamakon tunowa da yayi dawowar sa daren jiya da faduwar da yayi a harabar lambun sa wanda daga nan bai sake sanin inda yake ba a sakamakon kakkarfan baccin da yayi awon gaba da shi a wurin a yashe , da hakan baya rasa nasaba da sabuwar sumfurin dahuwar burkutun da ya sha a jiyan wanda gaba ɗaya ta hargitsa masa ƙwanya . Aina ka tarar da ni ? Shine kawai tambaƴar daya jefawa tafeedah bai koh kula da irin kallon da tafeedan ke jifan sa da shi ba mai cike da tarin ma'anoni . A jefa a inda kaga yafi dacewa da kai cikin kuma irin yanayin da ka zabarwa kan ka ."amsar da tafeedah ya bashi kenan " yana me miƙewa cikin yanayi na nuna alamun tafiya yake da niyyar yi ," Wani boyayyar ajiyar zuciya biyamuradi youssouf ya sauke a sakamakon fahimtar da yayi cewa tafeedah ne ya kawo sa ɗakin nasa ," Da misalin karfe nawa ka shigo gidan ? Su wa ka tarar a haraba ta ina nufin ma'aikata na sun yi chanji ? Mts! Idan kasan kana gudun zubewar mutuncin ka me zai sa ka jefa kan ka cikin rayuwar da kake youssouf ," tafeedah ya furta hakan cikin ƙufula yana me komawa ya zauna a inda ya tashi ," Cigaba yayi da cewa karfe uku na asubah na shigo sashin ka bayan tasowata daga wurin taron mu (meeting) ,inda masu tsaron gidan suka tabbatar min kana ciki tun farkon dare ," Amma abun mamaki nazo na gama neman ka ƙasa koh sama baka nan har nayi niyyar fita na sanar da masu tsaron ka , sai nayi tunanin zagayawa har cikin lanbu inda na tarar da kai kwance a ƙasa , da farko na tsorata amma daga baya na fahimci abun da ka min alkawarin ka daina sha kayi min rantsuwa da Allah akan baza ka sake sha ba ita ka sha youssof , ƙarin abun takaicin ma a cikin gidan nan , bayan ka san duk cikin ahalin gidan nan babu wanda ya taɓa sanin kana ta'amali da barasa ," kafi kuma kowa sanin masifun da fallasuwar wannan mummunar ɗabi'ar taka zata iya jawowa a garemu baki ɗaya ,"haba youssof , haba youssof , duk cikin tarin ababen zubda mutunci da jawo tozarta ka rasa wanda zaka zaɓa sai BARASA ? Bayan kasan itace shugaba ummul'aba'isi na jaan ɗan adam ga aikata kowanne irin sabon ubangijin mu ," tsagaitawa yayi lokacin da yaji muryar sa ta fara karkarwa alamun gaf yake da fara kuka sakamakon ƙona masa zuciya da wannan ɗabi'ar ta abokinsa ,amininsa kuma ɗan uwan sa youssouf da ya jefa kansa a ciki tun yana da ƙarancin shekaru sosai domin shi da kan sa ba zai iya cewa ga lokacin da youssof ɗin ya fara shan barasa ba , kawai dai ya farga ya gane ne shi da kan sa a saboda kusancin da suke da shi da juna ta yadda wasu lokutan dayawa zai taradda da youssouf ɗin cikin maye ," wanda tun yana ƙaryata kan sa cewa youssouf giya yake sha ,a dalilin tsawaita bincike da yayi bai taradda alamun barasa ba a duk inda youssouf ɗin yayi bigire da kuma boye masa tare da waskewar da ya dunga yi , har dai ya zo ya yadda, kuma yayi amanna aminin sa mashayin giya ne , ya kuma tabbatar lokacin da ya bi shi har zuwa wani tsohon kuchakin gidan saida burkutu wanda yake chan tsakiyar unguwannin talakawan gari inda anan youssouf yake zuwa yayi tatul , amma baya guzurin ta . A ranar yayi kuka har kan sa yayi ciwo ,kuma ya girgiza matuka musamman da yayi duba ga matsayin youssouf a garin na kasancewar sa ɗan sarki mai jiran gado , wanda ake sa ran watarana shi zai jagoranci dubannan al'ummar yankin ya zama shugaba a gare su abun koyi , Yaya hajiya umma (mahaifiyar sa) da mai martaba ,haɗi da ƴan uwan sa zasu ji a lokacin da suka farga , uwa uba yaya al'ummar gari zasu dubi lamarin yayin da labarin ya bazu ga kunnuwan su , haƙiƙa maƙiƴan sarari da na boye zasu ji daɗi suyi murna , sannan kuma da akwai yiwuwar subucewar samuwar mulkin jahar maraɗi daga hannun sa domin rashin chanchantar sa ta wannan fuskar ! Wane irin mulki ake zato ga mashayin sarki ???? Tun daga lokacin tafeedah ya nuna cikar amintakar dake tsakanin su da biyamuradi youssof ta hanyar yi masa faɗa da nasiha mai tsanani a kullum, gami da boye masa sirrin sa tare kuma da toshe duk wata hanyar da zata iya sa asirin youssof ɗin ya tonu , sosai yake koƙarin kare masa martabar sa da mutuncin sa , ta inda har ta kai yasamu nasara a wani dare shekaru biyu da suka wuce ,biyamuradi youssouf ɗin yayi masa alkawarin daga ranar ya daina shan barasa bayan fada da suka yi kacha-kacha inda tafeedah har yayi wa youssouf ɗin barazanar daina shiga sabgar sa idan har ba zai daina ta'amali da barasa ba . Farin ciki tare da kwanciyar hankali suka wadata ga tafeedah bayan jin alkawarin da youssof yayi masa ",cikin rashin sanin tuban muzuru youssouf ɗin yayi ya kuma ninke sa a baibai domin daga ranar ya sauya lokutan shan barasar sa muddin yana cikin garin maraɗi , ta yadda ya maida tsakanin sulusin dare lokacin fitar sa ya sha abar sa , yayin da idan yana wata ƙasar koh wata jahar a duk lokacin da ya samu sarari yake zuwa ko'ina ne ya nemo barasar gargajiya da aka fi sanin ta da " *BURKUTU* " zazzafa ya sha iya shan sa babu abun da ya fasa . Janye idanun sa da suka ciko da ƙwallar takaici tafeedah yayi , cikin rashin kuzari ya sake miƙe jin youssof ɗin ya rasa abun faɗa , toh me ma zai faɗa masa ? Soke hannayen sa yayi cikin wondon sa ,"ni zan shiga na gaishe da hajiya umma daga chan zan wuce ,sai kuma Allah ya kaddara saduwar mu , ina mai fatan Allah ya kiyaye ka ya baka nasara akan waɗanda zaka tunkara ," Daga haka ya sanya kan sa gaba da sauri youssof ɗin ya miƙe daga kan dardumar da ya idar da sallar sa ,"Jira ni nima babu abun da zan yi da wuce wanka sai mu fita tare ," bai jira amsawar sa ba kamar yadda shima tafeedah bai tsaya domin saurarar sa ba ya sanya kai yana me ƙarasa barin katafaren ɗakin youssouf ɗin . Yana shiryawa yana tunanin maganganun aminin sa tabbas duk wasu kalmomin da ya ɗauki shekaru yana furtawa agare shi gaskiya ne ," kuma shima a karan kansa yana mai bakin cikin halin da ya wayi gari ya tsinci kan sa a ciki sannan yayi iyakacin kokarin sa dan ganin ya daina shan burkutu amma hakan ya gagareshi duk kuwa da addu'o'in da yake yi a koyaushe yayi sallah akan Allah ya yaye masa, amma abun kamar tiri , ji yake idan bai sha burkutu ba a kowacce rana , yana iya rasa numfashin sa , burkutu ta zama jinin jikin sa , mahaɗin rayuwar sa kuma abar dake samar da nutsuwa da farin ciki a rayuwar sa ( a ganin sa kenan ) Ajiye matajin hannun sa yayi bayan ya kammala taje ƙwantatciyar sumar sa wanda yake yawan yi mata saisaye luf-luf da ita ," yayi yawo da idanun sa a ɗakin cikin son gamsuwa da bai bar wani abun sa mai muhimmanci ba ,"duk da cewa tun a daren jiya sojan dake kula da shirye-shiryen tafiyar tasa ya kammala haɗa masa kome cikin umarnin sa da yake zaune a gefe yana gwada masa abubuwan da yake bukatar tafiya da su ,"ya shirya su tsaf tare da kai su motar da aka shirya zai yi tafiya zuwa Niamey inda daga nan zasu daga zuwa Nigeria. Cikin takun sa na ƙasaita wanda yake bayyana cikar jarumtar sa irin na gwarzon soja , jaan tunga yayi ya tsaya "ɗan mitsitsin murmushi yayi ganin tafeedah da yayi a zaune cikin ɗaya daga cikin kujerun falon fuskar sa kadaran kadahan ya dago ya dube shi gami da miƙewa tsaye yayi gaba ," da sauri ya bi bayan sa suka jera . Cikin nutsuwa suka yi sallama a babban falon hajiya umma , da ya jawo hankalin siyama da merama aisha da suke zaune bisa wadatattciyar darduma suna ƙarin kumallo ," gefe guda masu hidimar zuba musu abincin da tsaftace wurin ne suke durƙushe zaman jiran su kammala , zumbur aisha ta miƙe Da ɗan gudu da tsalle ta ƙaraso gare su dai-dai lokacin da suke yiwa kan su mazauni akan jerun kujerun falon ,"zama tayi a gefen biyamuradi gami da ɗaura kan ta bisa kafaɗun sa ",barka da safiya hamma nah , nayi kewar ku sosai na same ku lafiya . ? Shafa kan ta yayi lokaci ɗaya fuskar sa tana sake faɗaɗa da yalwatatcen murmushin da yake bayyana tsananin  ƙaunar sa ga ƙanwar tasa yace ", lafiya lau meramar mai martaba yaya karatu ? Yaushe kika zo ? anyi muku hutu koh ? Anyi hutu hamma jiya da yamma nazo . Ɗan gyaran murya tafeedah yayi , Murmushi ta sake yi tana me sunne kanta a jikin hamman nata tace ,"ina kwana hamma tafeedah na same ku lafiya ," ?     Bazan amsa ba tunda abun ma wariyar launin fata ce ,"     Leƙo shi tayi ta bayan biyamuradi tana ɗan murmushi tace yi hakuri hamma tafeedah kasan nayi kewar hamma na watanni uku fa ,"     Kallo yake mata me kama da harara amma kuma fuskar sa ɗauke da sassayan murmushi wanda sai shi ya san ma'anar sa , sai kuma ita da duk lokacin da yayi mata irin wannan murmushin da kallon take tsintar kanta cikin wani irin yanayi na fargaba da mutuwar jiki ," Cikin sanyin jiki siyama ta ɗago idanun ta tana mai sauke su akan abun ƙaunar ta ," hamma youssof antashi lafiya ,? Hamma tafeedah barka da asuba ,? Ciki-ciki ya amsa mata da "lafiya" saɓanin tafeedah da suka gaisa sosai cikin sakewa har ma yake tambayar ta akan lamarin aikin ta inda ta tabbatar masa da ta ɗauki hutu na tsawon sati uku ," cigaba tayi da satar kallon biyamuradi da aisha wanda suke hirar su ƙasa-ƙasa cikin tsantsar shaƙuwa da kulawa da junan su da alama wata matsala ce da aishan wanda ta ƙagautu ta haɗu da yayan nata ta faɗa masa kasancewar ta rainon sa kuma abokin shawarar ta , cikin nazari take kallon sa bata samu ƙwanciyar hankali na sosai ba sai da ta fahimci faɗuwar sa ta jiya da dare bata haifar masa da wani rauni ba ,"ta sauke boyayyar ajiyar zuci , tana me Ƙwaɗaitawa a ranta ina ma ita ce maƙale da kafaɗun biyamuradin yana sauraren ta cike da kulawa da ƙauna kamar yadda yake yi wa ƴar ƙanwar ta sa ," lokaci zuwa lokaci suna sakarwa juna murmushin yaƙe ita da tafeedah da rabin hankalin sa yake kan wayar sa domin idan da sabo yaci ace ya saba da yadda yake zama saniyar ware a duk lokacin da biyamuradi da aisha merama suka haɗu . Da yalwatacciyar fara'ar ganin ƴaƴan nata ta ƙaraso falon , cikin hanzari bayun suka yi jerin gwano suna masu isar da gaisuwar su ɗaya bayan ɗaya , kafin cikar mintuna biyu sun cika babbar dardumar da suka shimfiɗa da kawatattun kwanukan abinci na alfarma ,ficewa suka fara yi ɗaya bayan ɗaya bayan sun sake kai gaisuwa . Da murmushi take amsa gaisuwar yaran nata tare da tambayar su yaya suke ," Umartar aisha tayi da ta zubawa yayun nata abinci ," ita kuma tuni siyama ta zuba mata abubuwan da take tunanin zata so ,"ta ɗebo ruwa a wani kyakkyawan mazuɓi tare da kamo hannun umma ta hau wanke mata su ," cike da so da kauna take sanya mata albarka ," tana me sunkui da kai take amsawa da ameen umman mu . Bayan sun kammala cin abincin ne tafeedah ya miƙe bayan amsa wayar da yayi wanda saƙo ya iso gare shi ana neman sa ," ƙarasawa gaban umma yayi tare da yi mata sallama addu'a tayi masa tare da ɗaurawa da nasiha ta ƙare da gargaɗin sa akan idan har yana cikin garin maraɗi kar ya yanƙe zuwa wurin ta kullum koh da bayan tafiyar aminin sa , Tare da ladabi yake amsa mata da yi mata alkawarin ba zai ɗauke ƙafar sa daga sashin ta ba koh da youssof baya nan , sallama yayi mata tare da miƙewa ya fice bayan sun yi musabaha da aminin nasa . Bin sa yake son yi domin ya shawo kan sa amma bashi da kuzari koh kuwa bai tanadi kalmomin da zai yi amfani da su wurin wanke fushin da yake hangowa a idon tafeedan ba , dan haka ya bar shi ya sarara zasu  shirya a waya , domin sanin da yayi cewa shi da aminin nasa basa iya wani dogon fushi da juna , duk saɓanin ra'ayin su bai taɓa jawo musu fushi da junan da ya wuce awanni ishirin da huɗu ba , dole daya zai nemi daya koh da ta waya ne koh ta hanyar sakon kar ta kwana su shirya ," kaunar junan su daga Allah take ," Cikin son fahimtar samun saɓani a tsakanin su umma take bin su da kallo har lokacin da tafeedan ya bacewa ganin ta ," tasowa biyamuradi youssouf yayi gami da dawowa daf da ita tamakar zai hau cinya ,"riko hannayen sa tayi tana me murmushi tace ,"yarona tun kafin ka tafi ka fara bani kewa ƙwarai zan yi kewar ka bani kaɗai ba har mai martaba ma jiya ya ɗauki lokaci yana mitar nisan da zaka yi mana alamu sun nuna kiris yake jira ya janye alfarmar da yayi na barin ka tafiyar nan ," Tare da tsananin ƙaunar iyayen nasa da yake taso masa yana kokarin dannewa yace "umma na shekara tamkar kwana ce kamar yau zaku ga Allah ya dawo muku da ni ,'kuma a jiya mai martaba ya sanar da ni cewa duk lokacin da yaga dacewa zai dunga tashin mutane daga nan musamman suna zuwa dubo masa ni ,ko da shi da kan sa bai samu damar zuwa ba ," umma na nima zan yi kewar ku ya karashe zancen sa yana me "ɗaga tafin hannunuwan ta ya sunbata tare da sanya kumatun sa a tsakanin hannun ta ,"ya cigaba da cewa addu'ar ku ita nafi bukata domin ita zata min jagora zuwa kan dukkanin wasu matakan nasara akan tafiyar da na sa gaba ," Murmushi tayi tana jin yadda kowacce ɗakika ɗaya take ƙaruwa da yawan kaunar ta ga gudan jinin zuciyar ta ", baza mu gushe ba muna masu yi muku addu'a har sai lokacin da mai rabawa ta raba tsakani ," ta furta hakan tana me kokarin maida ƙwallar da take son cika mata gurbin idanu ," yi maza kayi harama yarona . Waiwayawa tayi ta dubi sashin da siyama take zaune wacce a zahiri take shafa fuskar wayar ta da ta jiƙe sharkaf da ruwan hawayen da yake ta ɗiga a bisa fuskar wayar ,"a dalilin matsananciyar kewar biyamuradi tare da wani karfin son sa da yake hanƙoro a cikin zuciyar ta , uwa uba damuwar ta da halin da biyamuradin zai iya kasancewa a ciki bayan tafiyar sa zuwa wata ƙasar , duk da cewa ba wannan ne karon sa na farko ba ,amma ita a gareta a duk lokacin da zai yi nesa da yin tozali ga idanun ta rauni ne sabo zuciyar ta take yi . Siyama ta kira sunan ta ,"na'am umma ,! Yi maza ki sa a fito miki da kayan naki a kai mota ku zo ku kama hanya kar rana tayi sosai ," Ta juya ga biyamuradi youssof wanda bai kai ga fahimtar kalaman mahaifiyar tasa ba , tace ", koh zaka yi magana ga hadiman naka "sojojin sa" tun da su suka san shirin motocin tafiyar ta ku , zu zo su ɗauki jakar siyama zata bi ka ku tafi tare zuwa niamey ɗin , ku kaita har gidan "ubbo" Cikin jirkituwar fara'ar fuskar sa yake kallon bakin mahaifiyar tasa lokacin da take rattabo masa bayanin , amma kuwa lalle yarinyar nan tayi bala'in raina sa , watau ma da shi zata haɗa hanyar ta duk tarin direbobi da motocin da suke jibge a gidan nan ta rasa waye zata nema haɗa hanya da  sai shi ? A fusace ya waiwaya bangaren da yake zaton take da niyyar gargaɗin ta da idanun sa amma wayam yaga bata nan . Cikin kwantar da kai yace ,"amma umma ni ba kai tsaye zan tafi zuwa niamey ba zamu tsaya a wasu wuraren me zai hana direba ya kai ta ? Cikin ɗan ɗaure fuska umma tace ,"ko ma ina zaka biya tun da dai niamey ɗin ka nufa tare zaku tafi hankalina zai fi kwanciya sanin tana tare da kai cikin tsaro fiye da idan direban gida ne zai kai ta ," kayi musu umarni a zo a fito da kayan ta , Bai samu zarafin amsa mata ba ya hango fitowar siyama wacce ta sauya shigar ta daga doguwar rigar da take jikin ta a ɗazu ,zuwa wani sassalkan leshi ruwan madara wanda aka yi masa ɗinki riga buba da zane ta ɗaura ɗankwalin ta ya zauna mata ɗas akan tarin bakin gashin ta irin na fulanin usul , sosai kayan suka haska mata fatar ta me dauke da matsaicin haske ,zanen kuwa ya zauna ɗabas a cikakken kunkumin ta ,kafafun ta sanye cikin takalma marasa dunduniya bakake , hannun ta ɗaya rike da bakin mayafin ta ɗaya hannun kuma ƴar ƙaramar jaka ce da kallo daya za'a musu asan tare aka ƙera su da takalman kafafun ta , Cikin takun ta na rangaji wanda ya dace sosai da zubin ta na doguwar mace samɓal take takowa bayan ta bayun ta ne biyu biye da ita ɗayar rike da jakar kayan ta ɗayar kuma ta riko jakar da take ɗauke da computer ta da kuma wasu tarkacen takaddun su na likitoci ," Wani banzan kallo me tafe da sumfurin harara iri daban-daban da biyamuradin ya watsa mata lokacin da take ƙarasowa falon shi ya sa ta kusa faduwa ba shiri ta ɗauke idanun ta da tsautsayi yasa ta jefa su cikin nasa ta mayar da hankalin ta kan ummu wacce take ta faman sakar mata murmushi ,"umma na fito ," A fusace biyamuradi ya miƙe gami da yiwa umman sallama tare da tabbatar mata cewa zasu kasance akan waya a kodayaushe ," ba tare da ya sake kallon sashin da take tsaye ba ya sanya kai ya fita a karkashin rakiyar addu'o'in mahaifiyar sa . Risnawa tayi tare da yiwa umman sallama wacce take jaddada mata da ta kula kan ta , kuma ta tabbatar bata wuce iyakacin kwanakin da ta ɗiba zata yi ba a karshe ta ɗora mata da tarin addu'o'i ,"maza je ki kar su jira ki Allah ya kiyaye hanya ," Da gudun ta , ta karaso har tana ɗan haki jikinta rigar wankan ce sai katon tawul ɗin da ta rufu da shi ,"kar dai hamma nah ya tafi ta furta hakan tana mai taro ƙwalla cikin idanun ta ," Ba tare da siyaman ta amsa mata ba ta ɗaga kafafun ta tana me ƙarasa ficewa daga falon tana jin lokacin da hajiya umma ta fara rarrashin aishan wacce ta ɗauke ta tamkar ƴar cikin ta ba ƴar kishiya ba ," Ta ɗauki tsawon mintoci biyar a tsaye gaban jerun gwanon motocin su biyar bayan da tun fitowar ta wani soja ya amshi jakankunan hannun bayun ta ya sanya su a bayan mota, bayun suka koma suka tsaya daga bayan ta sanin cewa basu da ikon tafiya su bar wajen har sai idan ita tayi musu umarni koh kuwa sun ga tafiyar ta . Bangaren sojojin su ma suna ƙarƙashin umarnin ubangidan su ne wanda yake cikin ɓakar motar sumfurin ( purchase ) mai ɗauke da ɓakaken gilasai daga shi sai direban shi , ya shaƙa har iya wuya , a saboda haɗa hanyar sa da ta siyama , sosai yake jin zafin yarinyar shi da kan sa kuma ya rasa dalilin hakan kullum abun sake gaba yake , Sai da ya mula dan kan sa ya ɗago ya kalle ta yadda har ta fara haɗa gumi a ƙwaleliyar ranar damina ," yayiwa direban sa umarni da ya buɗe mata gidan gaba ," Cikin nutsuwa tayiwa kanta matsugunni a gaban motar tana me sauke ajiyar zucin wahalar tsayuwar da tayi , karaf suka haɗa ido ta mudubin gaban motar , da hanzari ta janye idon ta , dai-dai lokacin da direban ya tada motar ,sauran motocin suka bi bayan su , Suna gaf da barin gari ya cewa direban nasa ,"agades muka nufa ",  cikin cika umarnin ubangidan sa ya amsa gami da karya kan motar ya ɗauki hanyar da zata kai su ga hawa titin katsina ,zuwa zender ,sannan yankin agades ," Ɗas ! Kirjin ta ya buga ta maimaita kalmar ',Agades ' me kuma zasu je yi agades su da suka nufi niamey wannan wane irin bahaguwar tafiya ce mai kwan gaba kwan baya ,a maimakon ayi gaba an sake nausawa baya ,? Gimbiya maimouna ta garin agades ", sunan da yayi amsa kuwwa kenan cikin ƙwaƙwalwar ta , Tabbas yankin su maimouna suka nufa , hakan yana nufin biyamuradi wurin budurwar sa yake nufin zuwa tare da ita ,! Tunanin ta ya katse lokacin da ta tsinkayi muryar sa yana yin waya " hello Princess , dan kyakkawan murmushi ta hango saman fuskar sa,"da ya bata tabbacin wata kalma aka furta masa me daɗi," "Gamu bisa hanya,' ", ameen sai mun iso je t'aime ", .   Ji tayi ran ta yana tuƙuƙi ,kwantar da kan ta tayi gami da lumshe idanun ta ranta cike taf da tunanin gamuwar su da gimbiya maimouna tana kuma saƙawa da warware yadda zata yi amfani da duk wata damar da zata iya zuwa mata wurin yaƙin neman ƙwato biyamuradi youssof daga wurin kowacce mace , kamar yadda tun farko ta tsara wannan tafiyar tata zuwa wurin 'ubbo' da nufin fara dasa harsashin ginin ta ... Toh fah! # *vote* # *comments* # *share* *THANKS* [6/24, 9:59 AM] +234 701 013 7848: Fikrah writers association *MAFARI.......* _( Hargitsin rayuwa_ ) *Umm'muaz* 8 Miƙa tayi bayan ta ya bada sautin "ƙaƙas" sakamakon zaman awanni baƙwai da tayi wanda zata iya cewa wannan ne karon ta na farko da tayi doguwar tafiya irin haka a mota ," Wara idanun ta tayi sosai tana bin jerin gwanon bayin da ba sai an mata bayani ba tasan bayun yankin masarautar agades ne ,"cikin ranta kuwa mamaki fal take na ganin irin didima tare da sarewar da ake busa masu ,"wanda ya bata tabbacin anyi shiri sosai domin taryar biyamuradi,  nan take taji wani malolon bacin rai ya tokare ta a maƙoshi ., Bata fargar ba sai gani tayi bayun nan sun jagoranci biyamuradi zuwa ainahin cikin ginin masarautar wasu ta baya wasu ta gefe da gefen sa ," yayin da sojojin sa suka dakata daga inda suke ," Ganin haka ya sa cikin sassarfa ta soma taku tana bin bayan su da har suka riga suka danna kan su cikin shigifofin gidan  ,"cikin ranta kuwa tarin nadama tare da bakin cikin biyo biyamuradi take ,"wanda duk da sanin cewa da tayi basa shiri amma bata zaci kiyayyar sa da walakancin sa sun kai har haka ba a gare ta , duba da cewa tun da suka ɗauko hanyar tafiyar awanni bakwai koh kalmar sannu bata sake haɗa su ba ,"sai ita da  take ta faman satar kallon sa haɗi da sauraron amon muryar sa ," Basu yi wata tafiya mai nisa ba a faffaɗan filin da yake mazaunin harabar gidan sarautar wanda yake rairayi ne tas-tas lallausa ,da ya ɗauki yanayin damina da sanyin la'asar yake bada wani irin sanyin ni'ima da kamshin ƙasa mai sanya nishaɗi a zukata ., Amon sautin muryar biyamuradi taji ,"wanda ba ta kai ga fahimtar abun da yake faɗi ba , sai dai ta fahimci umarni ne ya basu ganin wasu tsiraru daga cikin su sun juyo gami da ƙarasowa gaban ta da take da ɗan tazara da su ƙadan ," "Ranki shi daɗe yarima yai umarni da a sada baƙuwathei ga shigifar gimbiya " Gyaɗa kai tayi yayin da dogarawan nan uku suka shige gaba ta juya ta bisu a baya tana waiwayar tawagar biyamuradi wanɗanda suka nausa shiyar gabas ba tare da ta samu arzikin da zata samu koh da kalma guda daga gwarzon nata ba ," Fiye da yadda tayi zato gini da tsarin masarautar agades ya tafi da hankalin ta tare da burgeta sosai da sosai ,"ware idanu tayi tana bin kowanne zane da taswirun da aka ƙawata bangon kowacce shigifa da ita ,da kallo mai bayyana shauƙi tare da burgewa ," kafafun ta da suke babu takalma tun a shigifar farko suna waɗakata cikin lallausan shimfiɗun alfarmar da suke ƙwance a kowacce shigifa," Cikin kowacce shigifar da zasu gifta bayu mata ne su huɗu suke zubewa gami da kai gaisuwa tare da tambayar inda suka nufa ,"amsa guda dogarawan suke badawa ."     Wagga diya baƙuwace da suke tafe tare da yarima biyamuradi ,kuma wurin gimbiya aka biɗa da a sada ta ," Har zuwa ga shigifar da tafi kowacce tsaruwa inda daga nan dogarawan suka juya bayan sun damƙa ta a hannun wata baiwa wacce tayi mata umarnin zama akan ɗaya daga cikin shimfiɗun alfarmar dake wurin ,tare da sanar mata ta jira gimbiya na nan fitowa bayan almuru ," Cikin takaici take duban baiwar da ta miƙe bayan kammala bayanin ta ,"    "Tou ki sada ni da inda zan yi alwala na kimtsa domin ina da bukatar yin haka , Siyama ta furta hakan ba tare da ta kai duban ta ga baiwar ba domin zuwa lokacin ta fara shaƙar takaicin halin ko'in kula da rashin girmamawan da ta fara hango alamun su ga hadiman gidan wanda ta hakikance ba kowa ya jawo mata hakan ba illa biyamuradi da ya danganta ta da matsayin Baƙuwa a gareshi a maimakon ƙanwar sa ƴar uwa ," domin ta tabbatar da ace ya kiraye ta da matsayin ƙanwa agareshi da tabbas ya samar mata da girma tare da matsayi a idanun hadiman gidan .,     Bayan idar da sallar ta "na magarib" tayi kimanin mintuna talatin tana zaune ,wanda har zuwa lokacin babu wacce ta sake bi ta kan ta cikin tarin bayun da suke ta kai kawo da manyan tire da tasoshi na alfarma a hannayen su waɗanda suke rufe ruf da mayafai iri guda masu launin ruwan sararin samaniya ", suna nufar wani sashi da ƙofar sa take rufe ta hannun dama , Cikin ta kuwa idan ban da ƙugin yunwa babu abun da yake ,"yayin da ita kuma ta sha alwashin baza ta sake tuntubar hadiman gidan kan wata bukata tata ba ," hasalima kishingiɗa tayi gami da lumshe fararen idanun ta ,gefe guda na zuciyar ta tana nazarin yadda lamuran suke tafiya ., Wani sassanyan ƙamshin turare ne ya fara bugar hancin ta kafin taji tashin muryoyin hadiman da suke cikin shigifar suna kirari tare da ƙwarzanta uwargijiyar su ," Ta ɗauki kimanin mintuna biyu kafin ta buɗe idanun ta a hankali ,"fes suka sauka cikin manyan idanun kyakkyawar budurwa da take zaune cikin shiga ta alfarma akan wata shimfida da ita bata san lokacin da aka samar da ita ba ,"kallon - kallo suka yi na adadin wasu daƙiƙai kafin siyama ta mayar da nata fatar idanun ta lumshe zuciyar ta kuwa bugawa take ɗas,ɗas,ɗas , tabbas wannan ce gimbiya maimouna , babu shakka ta amsa sunan ta ,' ganin ta kuma ya zo dai-dai da jin labarin ta ," sai dai koh kusa bata ji ta karaya ba bata ji ta tsorata ba ,sam ƙwarjinin ta bai ɗimautata ba ," hakan ya sa ta cigaba da lumshe idanun ta tamkar mai bacci wanda babu wanda ya lura da buɗesu da tayi ta rufe sai ita gimbiya maimouna wacce hasken lantarkin da yake tarwai ya bata damar hango cikin ƙwarar idanun siyama wacce bata kai ga sanin wacece ba hasalima bata san da zuwan ta ba ,"   Gnala wagga ɗiya daga ina ta tahou ?    Wacece ita ? Gimbiya maimouna ta furta hakan tana mai kai duba ga inda siyama take kishingiɗe Cikin girmamawa wacce aka kira da "gnala" ta amsa       "afuwa take biɗa , wagga ɗiya baƙuwa ce da suke tafe tare da mai girma yariman maraɗi tun da yammaci ta samu isowa nan ƙarƙashin rakiƴar dogarai su sunka isar da sakon wanzuwar ta anan daga bakin yarima ," Mayar da duban ta ta sake yi ga kyakyawar hausa/fulanin fuskar siyama ," nan take ta hango yanayin kamannin masoyin ta akan fuskar siyamar da take da tabbacin ba bacci take ba ,"ginshiri ne kawai tare da ƙasaita wanda ta danganta hakan ga kasancewar ita ma siyamar ɗiyan sarki ce kamar yadda tayi zato ,"siyamar ƙanwar youssouf ce wacce bata kai ga sanin ta ba , domin duk cikin tarin ƙannen sa da ta hakiƙance yana da su bai taɓa yi mata zancen kowa ba sai na "Aisha merama" ta kuma tabbatar ba ita bace wannan domin ya sha gwada mata hoton meramar maraɗi ," Nan take ta hango kuskuren da hadiman ta suka aykata na barin gimbiyar maraɗi bisa wannan shimfiɗar da bata kai ba a wurin ta . Gyaran murya tayi cikin yaren su na azbinawa tace ,"     Gnala a samarwa gimbiyar maraɗi kyakyawar shimfiɗa a wadata ta da abin sha da na ci haɗi da bigire mai kyau domin tayi wanka ta sauya kaya ta huta kafin mu gaisa ,wagga ɗiya gimbiyar maraɗi ce , kar a sake ayi wani abu na rashin ɗa'a da zai taɓa martabar mu har zuwa tafiyar ta ,ɗiyar girma ce maza a girmamata," Duk da cewar siyama bata jin yaren su na azbinawa amma ta fahimci zancen ta aka yi jin an ambaci "maraɗi "  Tunanin ta ya katse lokacin da taji hadima ngala wacce ga alamu ita ce shugabar bayin gimbiya maimouna," duba da cewa tun da gimbiyar ta fito duk sauran bayin suka kai gaisuwa tare da ficewa daga shigifar sai ita ta rage",  ta ɗurkusa tana ahuwa cikin girmamawa take neman iznin ta jagorance ta zuwa wata shigifar ," Ware ido tayi tana me sake tsuƙe fuska ta gƴaɗa kai ," abun mamaki kunnuwan ta sai suka tsinkayo mata ngala na mata ƙirari "ɗan murmushin gefen baki tayi tana mai bin bayan ta  ," Cak ta tsaya sakamakon sallamar sa da ta tsinta cikin amon muryar sa mai samar mata da kasala ," Waiwayowa tayi suka dubi juna ido cikin ido ,"dai-dai lokacin da gimbiya maimouna ta miƙe tana mai nufar sa cikin takun ta ," fuskar ta ɗauke da tattausan murmushin da duk cikin maza shi yayi zarrar samun irin sa ," Juyawa tayi cikin sauri ,kafin idanun ta su hango mata irin tarɓar da zasu yi wa juna wanda zai haifar mata da damuwar da zata hana ta bacci ," Cikin nutsuwa ta sauya kayan ta zuwa na barci bayan taci abinci ta getse ta sake yin wani wankan duk cikin ƙarƙashin kulawar gnala da take hidima da ita cikin girmamawa hatta ruwan wanka da kayan baccin ita ta haɗo mata ," yayin da a halin yanzu take kishingiɗe kan makeken gaɗon kwatankwacin nata sai dai wannan ya fi shi girma , gnala tana daga ƙasa ta miƙe bisa guiwarta tana tausa mata kafafu ," Tare da nazari take kallon ta tana son samo bakin zaren ta inda zata fara yi mata maganar da take son yi wato yi mata tambayoyi akan uwargijiyar ta ," sai dai kuma tana shakka akan koh zata samu haɗin kan gnala ɗin ," A hankali ta murɗa kofar ɗakin gami da shigowa ƙarƙashin rakiyar sassanyan kamshin ta mai shiga zuci ,cikin sabuwar shiga mai banbanci da ta ɗazu domin a halin yanzu sanye take da doguwar rigar siliki ruwan zaiba da duwatsun jiki suke ta faman ɗaukar ido ,miƙaƙƙen gashin ta ya zubo har gadon bayan ta yayin da madaidaiciyar fuskar ta mai ɗauke da manyan fararen idanu ta faɗaɗa da lallausan murmushi ," Sallama tayi musu tare da zama bisa gefen gadon da siyama take a zaune bisa a halin yanzu ," maida duban ta tayi ga gnala ,"           daɗa a bamu wuri mu zanta tare da ƙauna ta ,"        Toh ranki shi ɗaɗe ku tashi lafiya ɗiyan saraki , Barka da zuwa ƙauna ta siyama kin iso lafiya ? Yaya umma da fatan kun baro kowa lafiya kun iske mu lafiya ? Cikin murmushi siyama take amsa mata kafin daga bisani hira ta fara gudana cikin taka tsantsan daga kowaccen su ," domin ita ma gimbiya maimouna koh da ta tambayi biyamuradi youssouf wacece wacce suke tare ya tabbatar mata ƙanwar sa ce kuma sunan ta siyama ,sannan ita ma niamey ta nufa shiyasa tafiyar su ta zo guda ," Daga haka bai wani bata fuskar da zata sake zouwa mar da batun siyaman ba ," yayin da ita kuma hankalin ta yafi karkata ga batun tafiyar sa da yayi ta faman rarrashin ta da kyar ta amince suka rabu cikin aminci tare da alkawarin kasancewa akan wayar tafi da gidan ka a har kullum ,"      Ƙauna ta daga shigowar ki cikin garin mu zuwa saduwar ki da masarautar mu menene yafi burge ki yafi baki sha'awa ?    Ɗan jimm siyama tayi tana nazari "ga dama ta samu ," murmushi tayi tsarin ginin masarautar ku sosai ya burgeni , sannan na biyu girke-girken ku na gargajiya sun ƙawatar da ni kuma sun min daɗin ɗanɗano wanda har zan so na dunga samun irin girkin lokaci zuwa lokaci      Murmushi maimouna tayi jin siyamar ta yabi masarautar su ,idan kuwa haka ne zan baki baiwa ƙwararriya ɗaya daga cikin masu min girki ki tafi da ita zuwa duk inda zaki ta dunga yi miki irin girkin mu a duk lokacin da kika biɗa ," Cikin farin cikin ganin tarkon da ta ɗana yayi kamuwa kuma zuwan ta yayi alfanu domin zata tafi da wani bangare na kusa da gimbiya maimouna tayi mata godiya tare da yabawa akan karamcin da tayi mata ," Tare da nishaɗi gimbiya maimouna ta amsa tana mai jin daɗin zuwan siyamar domin ta daɗe tana son ta samu dama irin haka da zata tura wani na kurkusa da ita zuwa maraɗi "saboda wani boyayyan dalili nata ",  tunani ta fara yi cikin amintattun bayun ta wa zata tura ?       *GNALA*    Hasken alfijir ya fara haskowa ta tsakanin labulen tagar ɗakin nata ,tana zaune daga bakin wata doguwar kujera jal da take ɗakin nata da ta sha shimfiɗun alfarma , gefe daga ƙasa baiwar ta ce ngala        "zaki tahi zuowa maraɗi a matsayin kyautatciyar baiwa da na ba da ki ga ɗiyan sarkin maraɗi siyama ,"zaki tahi a matsayin mai yi mata girke girken gargajiya irin namu ," zaki yi duk wani kokari ganin kin samu mazauni mai kyau wurin sabuwar uwargijiƴar ki ,"ta yadda zata sau miki jiki ki samu shiga cikin lamuran ta wanda ta haka zamu san lamuran da suke gudana baki ɗaya a cikin gidan tun kafin wanzuwa ta ,"wanda hakan shi zai sa naji saukin tafiyar da dukkanin lamurana idan naje cikin su ," ba akan mutum guda zaki sanya ido ba akan duk wasu makusanta biyamuradi youssouf , nasan tsawon shekara guda zai ishe ki kammala aykin da na aike ki ," idan na zo babu wahala zan sauyawa siyama ke da wata baiwa daban ,amma a yanzu ke yafi chanchanta da ki tahi ," ki kula sosai bana so a samu matsala zan dunga tuntuɓar ki lokaci zuowa lokaci ,"   Cikin girmamawa da miƙa wuya baiwa gnala ta amsawa uwargijiyar ta ,"cikin ran ta kuwa tana tunanin wanne lamurra uwargijiyar ta ke son aiwatarwa a masarautar na maraɗi da har zai kai ta zaman aure da magajin garin ,???????? Kafin karfe baƙwai na safe siyama ta gama shirin ta ,an yi mata jagora zuwa sashin matan sarkin ɗaya bayan ɗaya ta kai gaisuwa inda a karshe tayi zango a fadar mai martaba sarkin agades inda nan ma ta kai gaisuwa tare da biyamuradi youssouf wanda shima yake shirye tsaf cikin shirin sa na tafiya," Ƙarƙashin rakiyar dogarai suka sadu da wurin da motocin su suke batare da bata lokaci ba suka shiga , sai dai a yau saɓanin jiya baiwa gnala ita ce a mazaunin mai zaman banza yayin da siyama take maƙale daga jikin kofa gefen biyamuradi wanda tun bayan gaisuwar su da ya amsa ita da gnala ɗin bai sake bi ta kan su ba bai kuma tambayi siyama wacece gnala ɗin ba ,"domin gimbiya maimouna ta gama yi masa bayanin kome ,"inda ta bayyana masa ayken ngla ɗin tayi zuwa niamey ,???( koh meyasa ta boye masa gaskiya )                          _______ Tafiya yankin azaba tabbas haka ne domin ba su suka sami isa niamey ba sai bayan magarib ," yayin da kai tsaye ya sa suka wuce gidan "ubboh" wacce tun jiyan take ɗokin zuwan ƙanwar ta mafi soyuwa agare ta ," Da gudu-gudun su suka fito ita da ƴan kyawawan yaran ta huɗu ," suka tarɓe su tare da jagorantar su zuwa ciki , inda ta miƙawa mai kula da hidimar gidan namiji ,"mukullin sashin da suke sauƙar baƙi ya buɗewa youssouf da muƙarabban sa sai dai biyamuradi youssouf ɗin ya dakatar da ita ta hanyar sanar mata da cewa karfe takwas suke da taro (meeting) kuma zuwa asubahin yau jirgin su zai ɗaga zuwa nigeria dan haka basu da isashen lokaci ," hakuri ya bata ganin yadda tayi kicin-kicin da fuska tana mitar bata lokutan da aka yi wurin shirya musu abinci shi da muƙarabban sa ,"ƙarshe dai dole ta sa suka kwashi abincin bayan ta sa anfito musu da shi ,suka yi sallama cike da ƙaunar junan su ,"domin duk da kasancewar su abokan faɗan juna amma wannan tsabtatatciyar ƙaunar ta tsakanin saƙo da saƙo tana nan tana gudana a tsakanin su ," koh sun yi faɗa basa jimawa suke shiryawa ba'a shiga tsakanin su ," Har ta ga ficewar motocin sa daga gidan tana ɗaga masa hannu zuciyar ta cike da ƙauna tare da tausayin ƙanin nata ganin irin aikin wahala da bautawa ƙasa da ya zaɓarwa kan sa ," Gefe guda kuma tana tinanin damuwar da ta hango kwance a ƙwarar idanun siyama cikin sassarfa ta juya gami da nufar cikin gidan ," koma meye dole zata magance mata matsalar ta saboda ita kam duniya bayan mahaifan ta bata da kamar mahaifiyar siyaman har abada baza ta mance da ƙaunar ta ba ,"                          _____     Karfe huɗu da rabi na asubahi agogon niamey jirgin su biyamuraɗi youssouf ya ɗaga Daga "Diori Hammani international airport " zuwa nigeria ,inda karfe shiddah da mintuna arba'in suna cikin tashar jirgin sama na "Nnamdi Azikiwe international airport Abuja Nigeria ",...... Naso chapter nan tafi haka yawa, "amma ban samu dama ba, "kuyi manage da wannan din insha Allah mai yawan yana tafe, " Koh kun San comments din ku suna kadan? 😕ku Kara ku yunkuro a tattauna ku fada min ra'ayoyin ku akan abun da yake faruwa, da ma Wanda kuke hasashen zai faru a nan gaba, Domun nishadin ku nake yi. 😍 #vote #comments #share #son so #fkrh [6/24, 9:59 AM] +234 701 013 7848: Fikrah writers association *MAFARI........* ( _Hargitsin Rayuwa_ ) *Ummu'muaz* 9 Misalin karfe biyu na rana ya kammala da kome da ya shafi sabon wurin da zai fara aiki inda aka tura su shi da sojojin dake ƙarƙashin sa chan tsakanin bodar da ta haɗa nigeria da niger ta cikin jahar borno ," Karfe huɗu jirgin su na sojoji ya ajiye su a cikin garin maiduguri inda zasu kwana zuwa washegari su wuce inda suka nufa ," Tun isar sa babbar hedkwatar soji na birnin na maiduguri , hankalin sa ya tashi da ganin irin taron mutane maza da aka gaggarƙame cikin ɗakunan horo , a galabaice matuka , cikin azabobi da horo mai tsanani wanda a gaban idanun sa ma yaga an fidda gawarwakin jama'a daga cikin ɗakin horon da azaba ta kashe su ," Duk da cewa a matsayin sa na babban soja hakan ba bakon abu bane ,toh amma zuciyar sa ta taɓu da yaji daga bakin wani sojan nigeria cewa waɗannan mutanen , mutane ne waɗanda aka kama akan zargin suna da hannu wurin tada tarzomar boko haram da ba'a kai ga tabbatar da laifukan nasu ba ,sune a jibge a garƙame cikin horarwa da azabtarwa , yunwa da ƙishirwa ,rashin isashen muhalli ta yadda wasu a tsaye suke wuni , wasu a tsugunne ,wasu a tanƙware , wanda yawan su ya tasamma dubunnai ," Gagara samun nutsuwar zuciya yayi bayan ya koma masaukin sa ,zuciyar sa sai kai kawo take da tunanin san samar da mafita ga waɗannan bayin Allah waɗanda a zahiri akwai zalinci cikin irin wannan ajiyar da ake musu ,kamata yayi a miƙa su ga kotun ƙasa ta yankewa kowa hukuncin sa dai-dai da shi waɗanda basu da laifi a sake su , wannan hukuncin ajiye su ana gana musu azobobin da suke kai su ga rasa rayukan su yayi tsanani da rashin dacewa ," Har gari ya waye bai sake marmarin fita ba sai da suka tashi barin ainahin cikin garin maidugurin zuwa bakin bodar da ta haɗa nigeria da niger ta cikin jahar borno , a tare da shi da tawagar sojojin su na niger da kuma ƙarin wasu sojojin nigeria , zuciyar sa cike da tausayin al'ummar da sanadin boko haram ta ɗaiɗaice suka bar ainahin cikin garin na maiduguri . ******* Cikin kwanaki biyar ɗin da su yakaka da falmata suka ƙara cikin sansanin su basu tsinci kome ba sai tarin wahalwalun da suka sake jikkata gangar jiki da ruhin su ," Domin zuwa yanzu karfi da yaji su yakaka sun zama ƴan aikin matayen nan da aka haɗa su rayuwa a ɗakuna ɗaya da su," Ta bangaren yakaka matar da suke kwana tare wacce ake kira "fanne" ta maida ta baiwar ta wacce take yi mata bauta nata da na ƴaƴan ta , tun daga kan wankan yaran biyu har zuwa wankin bargunan su da kullum ta Allah sai yaran sun zabga fitsari , wankin ƴan tsirarun kayan yaran da koyaushe ba'a rasa shi da guntun kashi da fitsari wanda yakakan take shan wahala wurin wankin saboda rashin isashen ruwa da sabulun wankin ,uwa uba rainon yaran da suke kusan yini goye bisa bayan ta duk wata jigila da su take yi suna ɗane a baya , ta sauke wannan ta goye wancen ,uwar su kuwa tana chan cikin yaran mata tana zuba hira da ɗinkin hular ta ,"bata chas bata ass , Ga falmata kuwa duk da kasancewar ta miskiniya amma hakan bai sa ajus ta ɗaga mata kafa daga sanyata ayyuka ba ," tun farar safiya idan ta tashi daga kan shimfiɗar da a yanzu ita kaɗai ke kwana a cikin gidan sauron sakamakon irin azabar da take ganawa falmatan cikin dare ya sa ta hakure ta samawa kan ta salama daga ,zagi hantara ,hauri , mangari da mintsinin da ajus take buwayar ta da su cikin dare , ta bar kwana a gidan sauron ta komo bakin kofa tana shimfiɗa zanen ta tana kwanciya bisa ," amma duk da hakan ita ke lalubawa ta naɗe gidan sauron ta kuma ninke kayan shimfiɗun da ajus ɗin ta kwana a kai , bata bar ta haka ba kullum ita take ɗebo mata ruwan wanka a bokiti da na tsarki a buta , daga bakin famfo inda anan suke samun damar haɗuwa ita da yakaka wacce ita ma take zuwa ɗibo ruwan hidimar fanne da ƴaƴan ta , famfon baki uku ne rak da shi kuma idan aka tayar da injin bada ruwan karfe biyar na asubah zuwa karfe bakwai na safe ake rufewa sai kuma lokutan sallah da shi ma na ɗan kalilan ɗin lokaci ne sakamakon rashin man tada injin tare da rashin wutar lantarki  ," dan haka yaƙi ne tukuru yake tashi wurin kokowar ɗibo ruwan wanda mai karfi ke ture na ƙasa da shi ya samu ya ɗiba ,"ire-iren su yakaka kuwa da kƴar da suɗin goshi da faɗawa cikin dagwalo tare da jin ciwo take samu ta cikawa falmata nata kayan ɗiban ruwan "da yakakan take tsaida ta a gefe ta hana ta shiga turmutsutsun ɗibo ruwan"  ta kuma ɗibo nata , wanda mafi yawancin lokuta ake kashe injin bada ruwan akan bokitin ta ," hakan ya sa har yau da suke cika kwanaki shidda wanda yake dai-dai da kwanakin su bakwai da barin mahaifar su ,fatar jikin su bata ga ruwan wanka ba sai dai ɗaurayar kafafu da hannaye zuwa fuskokin su da suke yi da ruwan alwala ," dan haka duk suka bi suka sake hautsinewa tare da ficewa daga kamannin su ,suka zama yarkace yarkace tamkar sabbin mahaukata. Ɗan dama-daman yagana ce wacce daman ita ta ɗan fi su wayewa da buɗewar idanu saboda ta tashi a alkaryar da take da wadatuwar wayewa , dan haka bata yadda kowacce mace ta nemi taka ta, bata yadda tayi aikin bauta ga kowa , sannan kuma abokiyar kwanan ta ma yarinya ce budurwa sa'ar ta dan haka suke yin chanjaras daga ta nemi kawo mata wargi ," damuwar ta yanayin rayuwar da take gudana ne a wurin da yanzu ta tabbatar ba gidan gwamnati bane , wuri ne na kazo na zo rayuwa ce irin ta daga ƙwari sai gwaiwa ,kowa kan sa ya sani rayuwa ce ta nafsi-nafsi ,uwa uba rashin wadatatcen abinci ,da ruwan sha ba'a maganar kayayyakin gudanar da rayuwa irin ta yau da kullum kamar su sabulan wanka da na wanki ,suturu da sauran su ," wanda tun zuwan su bata ga alamun za'a taimaka musu da waɗannan ba ," ga fatara da ta addabe ta saboda rashin koh kwandala da take matsayin mallakin ta ," gefe guda na zuciyar ta tana tausayawa abokan tafiyar ta da a yanzu ta fisu ƴanci , ta kuma sha zama ta gwada musu yadda zasu ƙwaci ƴancin kan su daga hannun ƴan iskan mata azzaluman da suka maishe su bayin su , sai dai daga yakakan har falmata babu mai kumajin iya kwatarwa kan sa ƴancin saboda rangwamen wayewar kai tare da ƙarancin shekaru , ɗan gwara ma falmata idan ƙumu ta ƙuma mata kai ta kan iya yin hobbasa ta nemi matsera daga hannun ajus ɗin ta hanyan yi mata batar dabo ta gudu bayan ajujuwa cikin datti da guntun najasa tayi zaman ta ," amma ga yakaka babu fuss , akan ga ƙwanjin ta ne kadai idan aka taba mata sanyin idaniyar ta falmata a gaban idanun ta , amma akan kan ta kam raguwa ce ta kin ƙarawa ," Dan haka kamar yau da suke zaune su ukun turmus a cikin rairayin da ganyayyakin bishiyar darbejiya ya lulluɓe ,yagana ta dubi fuskar yakaka da take duk jirwaye da lollori "( abun ka da farar fata )     "Nikam yakaka wannan mawuyacin halin da muke ciki a sansanin nan namu ya isheni , domin ban hango ranar yankewar wahalar mu ba a haka muna zaune cikin rashin sanin makomar rayuwar mu ya kamata mu samarwa kan mu mafita tun kafin ta ƙure mana ,"  dan zunkuɗa goyon yaron da ke ɗane baƙe-baƙe akan bayan ta wanda iskanci ne irin na yara ya sanya shi sanya kukan sai an goya shi domin yana yawon sa da gudun sa ko'ina ,"    "Hmm yagana kenan toh wace mafita kike tunanin muke da ita , mu da bamu da kowa kuma bamu san ko'ina ba sai nan ɗin ? Ai ina ganin haka zamu cigaba da hakuri har zuwa lokacin da ubangiji zai sauƙaƙa mana domin nasan yana sane da mu ," ta karashe zancen tana mai kokarin maida ƙwallar da ta ciko mata a ido      Yangana ta nisa cikin kallon sashin da falmata take wacce gaba ɗaya ta maida hankalin ta ga gefen su tamkar dai idanun ta suna kallon wani wajen , da azahiri kunnuwan ta tarwai suke tana kuma sauraran tattaunawar tasu ,kawai bakin ciki da damuwa ne suke danƙare a kahon zuciyar ta      ",Amma ai kina ganin yadda wasu mutane dayawa a sansanin suke taɓuƙawa kansu wasu abubuwan ta hanyar kula da rayuwar su da ƴan kananun sana'o'in da suke , me zai hana muma mu yunƙura mu gwada sa'ar mu koh zamu samu damar taimskon kan mu da kan mu yakaka rayuwa a haka bazai yiwu ba ," Murmushin takaici yakaka tayi ganin yadda yagana ta hakikice akan batun neman sana'a       Yagana kin manta da ruwan ciki ake jaan na rijiya ? Ita kan ta sana'ar ai sai da jari ,mu kuwa bamu da ko sisi bamu da kadara toh aina kike tunanin zamu samu jari bare a kai ga batun fara tunanin sana'ar yi Nasan bamu da jari yakaka toh amma ai ga "kolo"(abokiyar kwanan ta ) ita ma bata da jarin amma tana bi tana neman aikin kwangilar yin ɗinkin hula ,ana biyan ta muma mai zai hana mu nemi kwangilar mu dunga yi koh zamu samu ɗan kuɗin biyan kananun buƙatu ? Jimm yakaka tayi cikin tunani a zahiri ita bata wani iya ɗinkin hula ba sai dai tana ganin bata da wata mafitar taimakawa kan su ita da falmata idan ba ta wannan hanyar da ƙawar kirki yagana ta zo da ita ba ," dan haka ta ɗago da murmushi dai-dai lokacin da falmata ta waiwayo su tana me kafe gefen da take jin muryar yakaka da ido ,"      Yakaka bata iya ɗinkin hula ba koh riƙe allura a soka bata iya ba, asalima a cikin wannan halin bautar da muke ciki ina yakaka zata samu damar da zata zauna ɗinkin hula , yakaka kar ki ƙarbi abun mutane ki zo ki ɓata musu abu ya zo ya zama rigima da muguwar rawa gwamma ƙin tashi mu cigaba da addu'a Allah zai kawo mana mafita ," Falmara ta furta hakan karon farko tana me jin ciwon rashin idanun ta da babu abun da zai hana tayi ɗamarar karba kwangilolin ɗinkin hula har sai ta samar musu rayuwar da ta fi wacce suke yi yanzu inganci ita da yayar ta domin babu dare ba rana zata duƙufa soka allura da zarewa koh da zata tsire ƴan yatsunta da allura ," sai dai tana jin baza ta iya barin yakaka ta yi ba saboda sanin irin tarin ayyukan da  suke jibge akan yakakan wanda mafi akasarin su na wannan azzalumar matar ne fanne " idan dai ba tsakar dare yakakan zata tashi yin ɗinkin hular ba bata hango tana da lokaci ba , tsakar dare kuma da wanne haske zata soka allura a matsayin ta na ƴar koyo ? Su da basu da koh ashana bare tocila ? Zata fi so yagana ta zo da shawarar wata sana'ar da ita ma za'a iya haɗuwa da ita ayi . Shiru ne ya biyo bayan katse musu hanzari da falmata tayi ,kafin yakaka ta yunƙura cikin karfin zuciya      " zan iya falmata , yagana yaushe zamu samu kwangilar ɗinkin hular kuma aina zamu samu ? Wallahi zan yi koh da a tsaye koh a durƙushe ne zan kuma koya na kware cikin karamin lokaci ni dai fatana mu samu na kan mu ," ta ƙarashe zancen tana mai kamo hannun yagana wacce tayi shiru tana jimamin bahagon halin falmata , Toh bari mu fara tuntuɓar kolo koh zata shige mana gaba domin ita ta san masu bada kwangilar saboda ta fimu daɗewa a sansanin ,"        _____ Saɓanin tunanin su yakaka akan saukin samun kwangilar ɗinkin hula sai ga shi har yau da suke kwanaki huɗu da fara neman aikin kwangilar ɗinkin hular ,amma koh hula ɗaya ta gagara samuwa a gare su , daga ita har yagana ,saboda kowa shakkar basu ɗinkin hular sa yake domin gudun kar su ɓata masa dan babu wanda ya tabbatar da ƙwarewar su , kamar yadda ita kolo tayi suna wurin ƙwarewa da saurin ɗinkin hula hakan yasa take samun kwangila sosai," Har dai yanzu da suka gama hakiƙancewa baza su samu ba ,"kolo wacce ita ma ƙwarai ta so su samu ɗinkin koh dan ɗasawar da suke ita da yagana a yanzu ,"      Mai zai hana toh ku nemi wata hanyar neman kuɗin yagana ? Cewar kolo           Kolo kenan ina muka ga jarin neman kuɗi ? kina ganin aikatau ma mun gagara samu .inji yagana wacce duk mamakin halin mutane na rashin taimako ya cika ta,   Akwai hanyoyin neman kuɗi mana ba iyaka ma mu da muke cikin birnin maiduguri ," Tun kafin ta ƙarasa yakaka ta tari numfashin ta toh ai kolo bakya ganin mu a kulle muke cikin sansanin mu ba'a kuma fita sai da dalili mai karfi kamar idan kana saye da sayarwa koh kuwa ka nemi iznin zuwa ganin wani naka cikin gari ka ci sa'a an bar ka    Idan dai har kun tabbatar kuna son fita domin zuwa neman kuɗi cikin gari ni kuwa zan muku hanyar da koh kwanaki nawa zaku je kuyi ku dawo idan ma kuma zuwa zaku dunga yi kullum kuna dawowa duk zan taimaka muku , ku dai da farko yanzu kuyi tunanin sana'ar yi , idan kun fitan Cikin zumuɗi yagana tace toh ai ke kolo da kike fita cikin garin ke zaki fi mu sanin sana'o'in da zasu dace da mu kuma wanda zamu samu , ni dai ko ma meye zan yi , haka kuma nasan kawayena ma zasu yi ta furta hakan tana mai maida kallon ta ga yakaka wacce tayi shiru kamar ruwa ya cita , cikin ran ta wasi-wasin fitar su daga sansanin su take da fargabar abun da ka iya zuwa ya dawo a matsayin su na ɓaki da basu san ko'ina ba ,muryar kolo ta katse mata tunani Toh kun dai ga ana aikatau a gidajen mutanen gari ,"ana bara , ana aikatau a gidajen saida abinci idan baka tare da ƙazanta ,ana yin aikatau har a cikin kasuwanni , idan kana so tashi biya idan kuma kana so biyan wata yanzu haka nima ina wanke-wanke da shara gidan wata mata amma tashi biya muke , kullum naira ɗari biyu take biyana kuma na ci abinci nasha ruwan leda ga kaya kuma tana bani  , bata tsagaita ba ta cigaba da cewa tun da ku baku da naƙasa zaku iya yin aikatau ita kuma ƙanwar ku tayi bara a bakin kasuwa wallahi zaku yi mamakin kuɗin da zaku samu akalla ɗari bakwai zuwa dubu ɗaƴa a kullum banda kuma kwancen kaya da za'a dunga baku da sadakar ɗanyen kayan abinci , Cikin nazari yagana da yakaka suke kallon kallo yayin da falmata tayi jugum ta ƙurawa guri ɗaya idanu tana tunani ,"     *Toh mana bari mu ɗan huta koh* ?😁😍     *Mu bar su Yakaka/Falmata/Yagana su yi tunani cikin tsanaki*     #Comnents #Vote #Share #Fikrh [6/24, 9:59 AM] +234 701 013 7848: Fikrah writers association *MAFARI.......* ( _hargitsin rayuwa )_ *umm'muaz* 10 Shiri yakaka take sauri-sauri , tana yi tana taya falmata yin nata shirin , cikin mintocin da basu gaza goma ba har sun kammala , duk da dai kayan su na jikin su da suka cire suka sake mayarwa amma bisa ga dukkan alamu da su da kayan nasu sun ɗan samu tsafta domin sun ɗan yi haske , hakan kuwa bai rasa nasaba da wanka da wankin da suka samu damar yi tun a dare jiya bayan da suka tsaida shawarar fara fita neman na kansu cikin gari a ƙarƙashin jagorancin kolo da yagana , Kamar yadda kolo ta tsara musu shine su yakaka da yagana kowacce zata fita neman aikatau , yayin da falmata kuma zata zauna a bakin kasuwa tayi bara ," Da farko yakaka bata amince da yin barar falmatan ba , turjewa tayi sam tace sai dai falmata ta bita inda zata samu aikin ta zauna ta dunga jiran ta har zuwa lokacin da zata kammala ayukan sai  su koma tare , abun da duk ta samu tayi musu hidima tare , kuma abun da duk ta ci , ta bawa falmatan , Sai dai ga mamakin ta firr falmata taki ta amince da tsarin ta , ta tsaya kai da fata akan lalle ita ma sai ta nemi hanyar taimakawa kan su wanda kuma hanyar a yanzu ɗaya ce ita ce yin bara , idan har kuwa baza ta amince tayi bara ba toh sai dai tayi zaman ta kawai a cikin camp domin bata ga amfanin bin ta da zata yi kawai ta zauna ba . Ala tilas ta amince mata domin gudun bacin ran ta,  da kuma sanin cewa baza ta iya fita daga camp ɗin ta bar falmatan ba , toh ta bar ta a hannun wa ? Ga larurar da take tare da ita , amincewar ta shi ya zama dole sai dai bisa sharaɗin baza su nisanta da juna ba , dole a tsukin gurin da falmatan zata yi zaman barar ta anan ita ma zata nemi nata aikin .                                 _____ Yakaka , falmata ku fito mu tafi mana kar muyi rana , kolo ta riga ta gama magana da mai tsaron kofa            ,"yagana ke furta hakan dai-dai lokacin da take ƙarasowa bakin kofar ɗakin da su yakaka suke ,"         Gamu nan yagana mun gama shiri sai tafiya ,"                cewar falmata fuskar ta ɗauke da yalwatatciyar fara'a a karo na farko da yagana ta gan ta cikin farin ciki kwatankwacin wannan , wanda bata raba ɗaya biyu murnar zasu fara dasa harsashin cigaban su ne a karon farko cikin tsananin rayuwar da suka tsinci kansu ,"     Hannunwan su sarƙe da na juna suke sanya kafafun su domin barin cikin sansanin su da suka wanzu a cikin sa tun ranar da suka shigo birnin na maiduguri , yayin da sashi guda na zuciyoyin su ke cike da fata tare da burin zuwa su nemo na kan su ,gefe guda na zuciyoyin nasu kuma fargaba ne tare da taraddadin yadda fitar ta su zata kasance ,      Sansanin su a bakin babban titi yake dan haka basu sha wahala ba wurin samun motar bus da take jigilar mutane zuwa kowanne sashi na garin ,       Kasuwa monday market         Kolo ta furta bayan ta tsaida wata kwaraɓabɓiyar motar bus da take ɗauke da mutane jingim a cikin ta ,"           Shiga muje         Cewar conductor ( karen mota ) wanda ya wangale musu kofar motar ,      Ni ɗaya ce zan zauna akan kujera su akan inji zasu zauna ,"           cewar kolo dai-dai lokacin da take shigewa cikin motar domin yi wa kan ta matsugunni ,"           Wata zamiya kondoktan yayi tare da zabura ya babbake kofar motar ,"         Nai gamma waɗannan ƙattin ƴan matan har su uku ne zasu hau kan inji  kut ? ,"       Kayi hakuri dan Allah yayana ka taimaka mana wallahi naira ɗari daya ce jal da ni , kuma ni zan biya musu domin su da ka gan su nan koh sisi basu da shi mu ƴan gudun hijira ne , " cewar kolo cikin marairaicewa da karya wuya ,"       Kai ina bazai yiwu ba malama waɗannan sun yi girma da hawa kan inji a jere su uku rus ,          ya karasa zancen yana me jifan su yakaka da kallon banza wadanda suka yi tsilli tsilli a tsaye cike da taraddadin ganin samu da rashi ,sanin cewar idan aka ƙi ɗaukar su toh fa babu su babu tafiya dole su koma cikin sansanin su .       Tsalle konduktan yayi ya ɗale motar gami da bubbuga murfin tare da cewa ",Muje oga,"       Tsaya tsaya nima zan sauka tun da baza ka ɗauke mu tare da ƴan uwana ba ,"  Burki direban motar ya jaa lokaci guda ya juyo cikin hargagi yake tambayar me ya faru ne ?       Konducto yayi masa bayani ," sake tambaya yayi akwai sarari ne akan injin ,"      Akwai sarari oga sai dai sun yi girma sosai mutanen da ke kan sit zasu takura sosai ,"      Wani banzan kallo direban ya wurga masa da jajayen idon sa ,"    Ganin hakan ya sa da sauri konducton ya sauka gami da buɗe motar , yayi wa su yakaka alamun kira da hannun sa saboda har motar ta ɗan gifta ,"          Miƙo kuɗin ku        Cewar karen motar lokacin da direba ya daidaita motar sa akan titi    Da sauri kolo ta miƙa masa tsohuwar naira ɗarin da ta gama shan wahala a hannuwan jama'a               Azabar zafin inji da zafin ranar da motar ta ɗauka suka haɗu suka sa su yakaka , falmata da yagana haɗa gumi kirshiɓ suna ta ɗiga , yayin da suka kasa zama wuri ɗaya akan injin sai mutsu-mutsu suke suna jin zafin ƙunar da injin motar yake musu a ɗuwaiwai , uwa uba yadda suka takura suka cure guri guda kamar "kifayen gongon" gefe guda ga warin da konducton yake wanda ya buɗe hannayen sa ya tokare ɗaya hannun dai-dai fuskar falmata wari da tsamin hammatar sa na barazanar sanya su haraswa ,"      Bayan tsawon lokacin da bai kamata ace sun yi shi ba daga tsakanin sansanin su zuwa bakin kasuwar , amma a sakamakon rashin kyaun motar ,tsufan ta da kuma tsayawa a sauke fasinja a ɗau wasu a hanya ,ya sa suka kusan shafe mintuna arba'in a kan hanyar da bai fi suyi mintoci goma zuwa sha biyar ba , "        Cikin jigata suka sauko daga cikin motar , fuskar kowaccen su na nuna wahalar da ta sha a yayin tafiyar ,"     Yawatawa da idanun su yakaka da yagana suke yi cikin mamakin ganin yawan jama'ar da suke ta hada-hadar su a wurin duk kuwa da cewa hantsi ne bai wuce karfe tara da rabi zuwa goma na safiya ba ,"     Toh ku zo mu tsallaka titi kun ga chan ita ce kasuwar monday market maiduguri ( ita ce babbar kasuwar da take ci a kullum cikin birnin na maiduguri )           kolo ke yi musu wannan bayanin . Ba ƙaramin ɗauki ba daɗi aka yi cikin turƙa-turƙa kafin su yakaka suka iya tsallaka babban titin na Ahmadu bello da yake daura da kasuwar ta monday market ba ,"                    BAYAN AWA ƊAYA Duk wani zagaye sun gama shi amma basu yi dacen samun gurin da zasu yi aiki ba a zagayen har ma da ainahin cikin kasuwar , kama tun daga kan masu tuwo-tuwon da suke ciki da wajen kasuwar har zuwa kan goge-goge koh jiran shago , hasalima wurare da dama da suka je korar kare aka yi mu su ,"   Yagana , yakaka , kun dai ga yadda aiki ya gagara samuwa a gare ku a cikin kasuwa , hakan ya sa ya zama dole ku shiga cikin unguwanni ku kutsa koh gida-gida da wuraren sayar da abinci na cikin gari koh Allah zai sa ku dace , ni yanzu gaskiya rana ta riga ta ɗaga aƙalla yanzu sha ɗaya da rabi ta kusa kun ga na riga na makara zuwa gidan aiki na , duk da dai cewa daga nan zuwa cikin unguwar da nake aikin babu nisa amma yakamata ace tun tuni ina bakin aiki kamar yadda na saba , saboda haka ni zan tafi idan ya so anjima da yamma mu haɗu a tasha inda mota ta sauke mu ɗazu , amma kafin nan ita falmata yakamata ta samu wurin zama domin yin barar ta domin kuwa babu inda ya kai bakin kasuwa samun sadakha , dan haka  mu matsa daga chan wurin gefen bankin chan ta tsaya ko ta zauna a wurin har zuwa lokacin da zaku dawo , ina mai tabbatar muku da zata samu kuɗaɗe sosai ,             Duk kalma guda da take fitowa daga bakin kolo dai-dai take da ƙaruwar luguden da zukatan su yagana ke yi , wannan fa shi ake kira " anyi gudun gara an tadda zago " toh su kuwa ina zasu fuskanta cikin wannan turmutsutsu da taron jama'ah ? Ta ina zasu fara dilmiyar da kan su cikin gari alhalin basu da tabbacin zasu iya gane hanyar da zata dawo da su nan mahaɗar ta su , wanda a zahiri cikin zagayen awa ɗaya jal da kolo tayi da su a tsukin kasuwar , a halin yanzu koh tashar da mota ta sauke su baza su iya komawa ba saboda kan su ya riga ya juye , ina ga batun kutsawa cikin gari cikin unguwanni , ai wannan zancen ma bai taso ba ,"   Kusan a tare su ukun suka haɗa baki gurin fara magana ," amma sai yakaka da falmata suka saurara domin bawa yagana damar faɗin abun da ke nata bakin duba da cewa ta fisu kusanci da kolo ɗin ,"     Kolo mun gode sosai da dukkanin dawainiyar da kika yi mana amma a gaskiya daga ni har yakaka babu wacce zata iya tunkarar cikin garin da nufin neman aiki ba domin kome ba kuwa dan gudun bacewa mu rasa hanyar komawa a matsayin mu na baki ," jaan numfashi tayi lokaci daƴa tana mai sake marairaicewa , dan Allah kolo ki idasa taimakon da kika yi niyyar yi mana ki yadda mu biki zuwa unguwar da kike yin naki aikin idan ya so sai mu shiga gidajen cikin unguwar mu nemi aikin koh Allah zai sa mu dace ?      Ɗan jim kolo tayi cikin nazari a zahiri bata son su yakaka su bita su ga irin aikin da take yi sanin cewa ta boye musu gaskiyar aikin nata , amma ita sosai take tausayawa musu musamman yagana wacce take da wani boyayyen buri akan ta , "        Toh shikenan ku biyo ni amma da sharaɗi ," kamar yadda kuka ce kun fito neman aiki ne dan haka baku da wani zaɓi akan irin aikin da zaku yi ,"domin unguwar da nake aikina ta sha banban da sauran unguwanni ," nan ne gaba kaɗan tsallaken titin nan ta karashe zancen tana yi musu nuni da wata hanya da ta gangara kwari ta miƙe sosai daga gaban su ,"   Ke kuma ta juya ga falmata muje ki zauna akan dutsen chan ki ɓuɗe hannun ki ki fara bara , kar ki motsa koh nan da chan zuwa yamma zamu dawo mu same ki ,",          Cikin rashin kuzari yakaka take taku domin raka falmata wurin zaman ta inda gefen titi ne daf da bakin kwalta kuma ta baya jikin bangon kasuwa ne da yake kewaye da shagunan saide-saide,  gefe da gefe duk masu saide-saide ne na kayayyaki iri daban-daban wasu sun yi kashi-kashi akan buhu da algarara wasu a wulbaro wasu akan tire ,wasu kuwa ƴan tebura ne da su ,yayin  da gaba kaɗan kuma wani babban gini ne mai kama da ma'aikata ( banki ) ,"      Dai-dai gefen wani ɗan tsoho mai sayar da kayan gwari suka cewa falmata ta zauna kan wani ɗan dutse ,'        Cikin nutsuwar da take halittar ta ta laluba ta ɗosana duwawun ta ,",      Durkusawa yakaka tayi akan guwowin ta gami da kamo hannunwan falmatan tace ,"        Falmata dan Allah ki kula da kan ki kin ga inda muka ajiye ki ɗin nan ki zauna kar ki motsa koh nan da chan ,          "ɗaga kan ta tayi ta dubi sama taga akwai rangwamen hasken rana sakamakon manyan giza-gizan da suke yawo suna kare ranar , " idan kin ji kishirwa ga wannan", ta kunce bakin zanen ta ta ciro wata tsohuwar naira goma wacce ita falmata bata san inda ta samu ba ," ki sayi ruwa da shi ki sha idan kuma Allah ya sa kin samu sadakha idan kin ji me tallar abun sayarwa ki sayi wani abu ki ci , sake damƙe hannun falmatan tayi tana me jinjina hannunwan su da suke haɗe da na juna , falmata kar ki je koh ina ki jira ni dan Allah , kuma ki kula min da kan ki ,"        Yakaka ni fa sauri nake da Allah ki taso mu tafi ," cewar kolo cikin gundura da doguwar maganar da yakakan take yi da ƙanwar ta ta , wanda ita da yagana ba jin abun da take faɗa suke ba sakamakon ƙasa da muryar ta da tayi ,ga kuma hayaniyar motoci da ta muryoyin jama'ah  ," Yunƙurawa tayi ta mike tare da cewa '" yi hakuri kolo mu tafi ,           idanun ta akan fuskar falmatan wanda a zuwa yanzu ta kasa fahimtar a wanne yanayi zuciyar falmatan ke ciki ,"    Tayi taku biyu ta ji hannun falmatan ya sarƙe a cikin nata ,"         ", Yakaka dan Allah kar ki ɗaɗe kuma ki lura da kyau da wurin da kuka ajiye ni kar ku manta wurin , sannan kuma kema ki kula da kan ki , Allah ya baku sa'a kije ki dawo ina jiran ki anan yakaka ,"            Daga haka ta zame hannun ta daga cikin hannun yakaka ta buɗe zazzaƙar muryar ta tare da ware hannuwan ta biyu ,ta fara rero kalmomin bara ,"        Alaro sadakah fisabilillah        Alaro sadakha fisabilillah Gurbin fararen idanun ta cike taf da hawayen da suke sheƙi a cikin hasken ranar , zuciyar ta kuwa ta jima tana kwararar da hawayen maraici da wata irin kewa maɗaukakiya ,"      Juyawa yakaka tayi cikin sassarfa tana mai bin bayan su kolo waɗanda har sun riga sun soma tafiya ," lokaci guda tana mai share ambaliyar hawayen da suke shatata akan farar fuskar ta , "zuciyar ta kuwa wani irin raɗaɗi da zogi suke yi mata tana jin kamar baza ta iya tafiya ta bar ƙanwar ta anan ba , tana jin kamar idan ta bar ta wani abu zai taɓa ta , " tana jin kamar ta kasa bata kariyar da ta kamata ,"  sai dai sashi guda na zuciyar ta yana mai karfafa ta da cewa ta tafi ai ZATA DAWO TA SAME TA ,' kuma a yanzu wannan hanyar ce kaɗai mafitar su domin tallafawa kan su .," da haka suka tsallaka babban titin da ya raba su da sashin kasuwa ,"      Dai-dai zasu gangara gangaren (kwarin) unguwar da zasu neman aikin ta sake waiwayawa a karo na barkatai tana me sake kallon bigiren da ta ajiye ƙanwar ta ta , chan ta hango wata mata ta miƙa mata wani abu da take kyautata zaton sadakha ce aka fara bata ," nan take fuskar ta ta yalwatu da kyakyawan murmushi har haƙoran ta suna masu bayyana cikin ran ta tana me yin hamdala , ,"lokaci guda ta sanya kafafun ta tare da tattare zanin ta suna masu sauka cikin kwarin unguwar da ake kiran ta da ,"BULABURIN",  unguwar da tayi ƙaurin suna a birnin na maiduguri gurin tara lalattun mutane , kama tun daga kan ƴan shaye shaye , karuwai da ƴan daba ," .         Assalamu Alaikum ina miƙa sakon gaisuwa ta ga masoyan rubutuna a duk inda kuke , tare kuma da baku hakurin jinkirin cigaban labarin da ake samu wanda a zahiri ba a son raina bane,  face hali irin na rayuwar ɗan adam wacce take tafe da cuta da lafiya ," duk tsawon lokutan da kuka ji ni shiru , shirun ya faru ne a sakamakon rashin lafiyar da nayi fama da ita , amma a halin yanzu Alhamdulillah da sauki ., Nagode #vote #comments #share #fikrh[6/24, 9:59 AM] +234 701 013 7848: Fikrah writers association *MAFARI........* ( _Hargitsin Rayuwa )_ *umm'muaz* 11 Fuskar ta ɗauke da murmushin da ya zarce zuwa dariyar da ta bayyana ƴan gajerun jerarrun haƙoran ta ,take shafa tare da sunsuna tarin kuɗaɗen da ta samu ta hanyar barar da ta shafe awanni fiye da uku tana zaune tana yi , wanda bata kai ga sanin yawan adadin kuɗaɗen ba ," Sake runtse kuɗaɗen tayi cikin tafukan hannayen ta ,lokaci guda kuma ta fara lalubar leɗar da ta saya awara taci ɗazu domin ta kulle kuɗaɗen nata a ciki ganin cewa kuɗaɗen sun taru a hannunta , zuciyar ta kuwa ƙwal kuma cike da farin ciki a rayuwar ta yau ne karo na farko da ta riƙe kuɗaɗen da suka kai haka yawa nata na kan ta , nan take taji ta sake gamsuwa tare da samun karfin gwaiwar cigaba da yin bara har sai yadda hali yayi , " Gefe guda kuma tana Allah-Allah su yakaka su dawo ta nuna mata irin ɗinbin alherin da ta samo musu ," Soke kuɗin tayi a cikin zanen ta bayan ta ƙulle su a cikin leɗar , ɗan saurarawa tayi tana mai jin yadda rugugin hadari yake bada amo bisa ga dukkan alamu garin gangame yake da hadari ,duba da yadda ta ji rangwamen zafin rana da yake nuni da cewa hadari ya kare ranar ," , Ji tayi hankalin ta yaɗan soma tashi sanin cewa a sararin Allah take ba cikin rumfa ba ,ita kuma bata shiri da dukan ruwan sama mummunan zazzabi da ciwon kai gami da tari yake samar mata ," Ɗan matsawa tayi ta gurin da take jin muryar dattijon nan wanda tun da ta zauna a wurin take jin sa yana hada-hadar saye da sayarwar sa ," Baba dan Allah ince koh hadari ne sosai haka a garin naji sai cida garin yake ? Ƙwarai kuwa ƴata hadari ne gashi nan ya shata bakikkirin a sama ," ya kamata ma kiyi haramar komawa gida ,'domin duk jama'a ma shirin tafiya suke ga la'asar ta riga ta gabato ," Tsugudi falmata tayi cikin fargaba tare da taraddadin rashin dawowar su yakaka har yanzu ," Tunanin ta ya katse ne lokacin da taji wata mummunar ƙara da tafi karfin a kira ta da rugugin hadari domin gabadaya sai da ta ɗimauce ,"lokaci guda ta miƙe a zabure gami da tsayuwa akan kafafun ta da take jin ƙasa na girgiza ," Waige waige ta fara yi lokacin da ta tsinkayo hayaniyar muryoyin mutane sun ƙaru tare da takun kafafun su da alama guje-guje aka fara ," Cikin tashin hankali ta sake matsawa wurin dattijon nan da take jin muryar sa sama-sama da alamun tashin hankali ,sai dai rashin jin isashiyar hausa da kuma yadda ta firgice ya sanya ta kasa tsintar koh da kalma guda daga cikin kalmomin da take ji a bakunan al'ummar wajen bare ta fahimta," Ba-Baba dan Allah meke faruwa ne ƙarar menene haka naji ? Ƴata bom ne ya tashi yanzu yanzu a post-office , maza maza ki kama hanyar gida domin kuwa kasuwar ma yanzu za'a rufe ta sojoji zasu zo ,ai yau gari sai yadda hali yayi bom a post-office matattarar mutane ? Kai Allah dai ya kawo mana karshen wannan masifa ," Kalmar bom da ta sojoji ita kaɗai falmata ta fahimta cikin dogon jawabin da dattijon nan yake mata ," a take wasu hawayen da bata san lokacin da suka samar da kan su ba suka fara sintiri akan fuskarta ," dai-dai lokacin da taji an kai mata wata bangazar da tayi sanadiyar zubewar ta a ƙasa da bata raba ɗaya biyu ƙaton da ya bangajeta gudu yake yi domin ya samu isa ga mafakar sa kafin zuwan sojoji koh kuma tashin wani bom ɗin ," Ji tayi dattijon nan ya sanya hannu ya ɗago ta lokaci guda yana me fada akan rashin imani na wasu mutanen ta yadda har wannan garjejen ƙaton ya bangaje ƴar ƙanƙanuwar yarinya kuma miskiniya amma bai koh juyo ba ," Ƴata ina abokan tafiyar ki da suka ajiye ki anan suke ?? Koh kuma ina ne unguwar ku ? Kiyi maza fa ki samu ki bar wajejen kasuwar nan dan nan da mintoci ƙaɗan kowa zai watse ," Yakaka , yakaka , itace kawai kalmar da bakin falmata ya furta ba tare da ta jira jin ƙarshen zancen dattijon nan ba , lokaci guda kuma ta fara jefa kafafun ta ba tare da ta san inda take sanya kai ba koh kuwa inda ta nufa ," ita dai burin ta ta sadu da yayar ta ," AWANNI UKU BAYA Tun da suka gangara gangaren unguwar yakaka da yagana suka ware idanun su sosai suna masu kallon tun daga kan tsarin gine-ginen unguwar har zuwa kan mutanen da suke cikin unguwar da mafi akasarin su kallo ɗaya za'a musu a fahimci ƙarancin tarbiyyar da take tare da su ," Unguwa ce irin ta yaku-bayi talakawa mafi yawan gine-ginen unguwar sun shiga ƙasa kana iya ganin kan ƙwanukan ,ƙananan gidaje da suke manne da juna ,waɗanda kallo ɗaya za'a musu a fahimci mutanen cikin su na rayuwar rashin wadata," Mafi akasarin matasan da suke yawo a unguwar irin ƴan shaye-shayen nan ne masu rabin kai a aske ga kuma uwa uba rangwamen tsafa da ta bayyana sarari a gare su , ,"duk tashin muryoyin su irin na ƴan maye ne da take tafe da amon kalmar arziki ɗaya ashariya goma ," Yaran su ƙanana kuwa kaso tara cikin goma yawo suke kafafun su babu takalma ,dauɗa ta samu mahallin zama na dindindin a jikin su da suturun su ," Ga Ƴan mata birjik waɗanda mafi yawa hannayen su zuwa kawunan su ɗauke yake da robobi zuwa bokitaye da fantekun ,ababen ci na sayarwa ," sun sha kwalliyar gazal da jar hoda ,laɓɓan su na ƙyallin jan baki 24 awa ,", Duk ba wannan yafi girgiza zuciyar yakaka ba asalima ita bata hango wani aibu koh naƙasu a tare da mutanen unguwar ba idan aka ɗauke ashariƴar da suke amfani da ita cikin maganganun su wanda hakan yake bakon abu a wurin ta ,sai dai duk da haka ta ɗauki hakan a matsayin wayewa irin ta ƴan birni duba da cewa ita a wurin ta wayayyun mutane ne ., Abun da yafi takura yakaka da firgitata shine yawan karnuka tare da ƙyanwowin da take ganin giftawar su a cikin unguwar tamkar dai yadda akuyoƴi da tumakai suke yawo a garin su wanda hakan babban barazana ne a gare ta kasantuwar ta ma'abociyar tsoron karnai , yakaka tana ƙin kare yadda take ƙin mutuwar ta koma fiye da haka , dan tabbas da tasan zata haɗu da karnuka irin haka da ko daga cikin sansanin su baza ta fito ba bare har ta ɗauko kafa ta shigo wannan unguwar ,", Ga bangaren yagana kuwa yanayin tsarin unguwar ne sam bai mata ba a zaton ta zata ga sun doshi unguwar hamshaƙan masu kuɗi ne ,"inda zata yi kallon birni sai take ganin su a wata ƙazamar unguwa wadda koh a garin su ba'a sanya ta cikin unguwannin arziki ba ,' duk sai ta ji tafiyar ta daina yi mata armashi ., Sun ɗan yi tafiya mai nisa kafin su jiyo Kiɗan da suke ji sama-sama yana sake cika kunnuwan su a yayin da suke dosar wani wajen matattara jama'ah shi yasa suka maida hankulan su suna bin mutanen da suka fara cin karo da su a farfajiyar wajen da kallo ," Da farko rumfunan sayar da abinci ne birjik a wurin wanda aka kafa manya-manyan murhu aka ɗora manyan tukwane lamba talatin-arba'in an babbaka wuta a ƙarƙashin su da basa raba ɗaya biyu girki ake ," Daga gefe cikin wasu rumfunan kuma shimfiɗun tabarmai ne da suke cike da mutane a chakuɗe maza da mata , ba'a jin kome sai tashin muryoyin su da dararrakin su ," Daga gaban su nan ne wata babbar kofa take wanda kuma daga cikin sa wannan kiɗan kalangun ke tasowa ," Ɗaya daga cikin rumfunan sayar da abincin nan suka ga kolo ta nufa inda su ma basu yi wata-wata ba suka bi bayan ta zungui-zungui , daga bakin rumfar ta dakatar da su yayin da ita kuma ta shiga ciki inda suke jiyo tashin muryoyin wasu mata ," Kichibus kolo tayi da uwarɗakin ta ,wacce kallo guda za'a mata a ajiyeta a mizanin tatattun karuwan mcmc, duba da yanayin shigar ta na wata matsatsiyar doguwar rigar wani yadi da ya cire kowanne bangare na jikin ta kashi-kashi a sarari ,"uwa uba koɗaɗɗiyar fatar jikin ta da duk man sauya kalar fata ya maida ta dabbare-dabbare , sannan zaƙo-zaƙon faratan hannun ta da suka sha fenti ruwan ɗorawa zuwa gashin ɗokin da ta yaɓa a kan ta launin shanshanbale ,wanda bata samu koh da zarafin ɗaura masa ɗankwali ba ," Wata harara ta watsawa kolo da mitsi-mitsin idanun ta da suka sha koren fenti daga sama ," ta tauna cingam ya bada ƙarar bas-bas-tas ," Dan ubanki kolo yau sai yanzu kika ga damar zuwa ? Duba agogo karfe nawa yanzu ? Karfe sha biyu saura , toh bari kiji wallahi a kuɗin ki zan cire dan ni ba'a min iskancin banza idan kin gaji da aikin ne sai ki faɗa na maye gurbin ki da mai so ," Kiyi hakuri madam wallahi na tsaya taya ƴan uwa na neman wurin aiki ne kin gan su chan ma tare muka zo domin basu samu gurin yin aikin ba ma ," ta ƙarashe zancen tana mai nuno su yagana waɗanda duk abun da yake faruwa tsakanin kolo da uwarɗakin ta suna ji sarai daga inda suke . Ɗan leƙawa madam ɗin tayi tayi wa su yakaka wani kallon sama zuwa ƙasa ," Ni dai na gaya miki zan cire kuɗin awa biyun da kika yi lattin su domin ni bana asara , " ki wuce ki kama aikin ki ," ku kuma "ta sake ɗaga murya yadda su yakaka zasu iya jiyo ta Sai ku shiga daga ciki domin kun yi sa'a jiya-jiya sally fara ,ta bada cigiyar a ƙaro mata ƴan aiki biyu a madafar ta domin cikin tsoffin da da suke mata aikin ɗaya shekaranjiya ta mutu," Turus yagana da yakaka suka yi duk da cewa sun fahimci abun da ta sanar da su toh amma inane cikin ? Kuma wacece" sally fara " ? Ganin yadda suka yi wiƙi-wiƙi suna kallon ta ya sa ta fahimci basu gane nufin ta ba ," ƙas-ƙas ta sake yi da cingam sannan tayi wani turanci ", Idiyot buladiful marafoka waɗannan ajawos ɗin koh fahimtata ma basa yi ," ke kolo koh kuma ma ke zauna kiyi aikin ki ɗanliti zo tafi da waɗannan garorin ciki wajen sally fara kace ga ƴan aikin cikin madafa an samu ," kai ku bishi dallah kun tsaya sai wani kif-kifta idanu kuke yi kamar an shaƙe akuya a mayanka idiyot buladiful Sum-sum su yagana suka bi bayan mutumin da aka ƙira da ɗanliti wanda tashin farko idan an hango shi yana tafe za'a zaci wata zarkaɗeɗiyar budurwa ce sakamakon shigar mata da yayi da yadda yake karairaya da lanƙwasa kamar tarwaɗa a cikin ruwa ,"uwa uba kwalliyar da ya rangaɗawa fuskar sa har da yari da ɗan kunne ," Suna shiga cikin babban harabar dodon kunnuwan su ya fara tsalle a sakamakon kiɗan gurmi da kalangu da suke tashi ," a babbar harabar da tafi kama da wata ƙaramar makaranta ," mata ne da maza waɗanda kallo ɗaya za'a musu asan mutanen banza ne suke ta kai kawo ," Wata ƴar hanya ɗanliti ya bulla da su sai ga su sun bullo a gaban wani waje mai kama da shagon cin abinci ga irin fararen kujeru da teburan su nan birjik a wajen ta tsakanin kujerun da duk babu kowa akai suka wuce suka fito wani babban fili wanda suka taras da wasu manyan murhu da Manyan yankakkun durum bisan su wasu mata na koƙarin haɗa wuta ," Wani wari da tsami kamar na ruɓaɓɓen abinci shi ya fara dukan hancin su kafin idanun su yayi tozali da wasu yamusassun mata ƙomaɗaɗɗu suna ta faman wanke jiƙaƙiyar ruɓaɓɓiyar dawa suna subda ruwan yana kwarara zuwa wata katuwar magudanar ruwa ," Larki , hema ,duduwa ina madam sally take ? Inji danliti ," Koh kafin su amsa masa sai ga wata koɗaɗɗiyar mace da take tsakanin shekaru arba'in da biyar zuwa hamsin ta fito daga wani lungu hannun ta riƙe da wani ƙaton luɗayin kunu da ya kai girman a haɗa kawunan yakaka da yagana ," Kai liti yaya anka yi ne eh ? Waɗanan ƙuya-ƙuyan kuma daga ina ? Daman madam jumai ce tace a kawo miki ƴan aikin ga su nan su biyu an samu ," ya ƙarashe zancen sa yana farfari da ido tare da yarfe hannu ," Ta ƙundumo wata ashariya ta makawa madam jumai ," kafin ta ce Waɗannan ƴan shilan ne zasu min aikin ciki ? Waɗannan ne zasu tuƙa min DURUM ƊIN BURKUTU  ? Tirƙashi waɗannan ai basu wuce suna bayan uwar su tana tatsa musu nono suna sha ba ? Wata dariya da ɗaya daga cikin matan da suke aikin wankin dawar nan tayi shi ya katse banbamin masifar da sally fara", take yi ," Kin ji madam sally da wani zance ai da rashin tayi akan bar arha da kuma rashin ƙira karen bebe ya bata , ban da abun ki ai gwada su zaki yi ki ga koh zasu iya ," bakya ganin kamar ɗaukar irin su ma yafi riba , zaki mori kuruciyar su da kyau kafin abar ta fara aikin ta , zasu daɗe suna yi miki bauta kina juya su sai yadda kika yi da su ? Ai madam kar ki bari wannan damar ta wuce ki ," ta ƙarashe zancen tana sakin wata sakaryar dariya lokaci guda kuma tana chafe amshin wakar ƙidan kalangun da yake tar-tar kamar a gaban su mai kalangun yake kaɗa gangar sa, " Ɗan jimm madam sally tayi kafin ta ce toh bari mu gwada ɗin da gwaji jirgin sama ya tashi ," cikin kallon sheƙeƙe ta juyo ga su yagana waɗanda suka yi jugum suna sauraran maganganun matan da sun yi jikoki da su da mafi yawancin zantukan ma ba fahimta suke ba ," dan haka sam basu kai ga fahimtar ma'anar kalmar BURKUTU ba ," Zan ɗauke ku aiki amma da sharaɗi idan naga baza ku iya ba zan sallame ku ," Cikin gurbatacciyar hausar yakaka da zuwa yanzu tafi yagana zaƙuwa da son ganin sun samu aikin yi tace Mama zamu iya kowanne irin aiki ne ki bamu zamu yi koh yagana ? Ta maida tambaƴar ta ga yagana wacce bata samu zarafin magana ba illah gƴaɗa kanta da tayi alamun sun amince ," Meye sunayen ku sannan kuma daga ina kuke ? Ina ne unguwannin ku ? Sannan ina da dokoki na , da farko anan zaku dunga kwana koh kuwa zaku dunga zuwa ne kuna komawa kullum ? Mu ƴan gudun hijira ne , Ni sunana yakaka ,kawata kuma yagana. Zamu dunga zuwa ne kullum , Toh kullum karfe tara zata yi muku anan wurin ,sannan zaku tashi karfe biyar idan masu aikin dare sun zo ," Suka amsa da toh , Sannan kuma tashi biya kuke so koh biyan karshen wata ? Suka haɗa baki wurin cewa tashi biya ," Zan baku abincin rana kaɗai zan kuma baku naira ɗari uku-uku kullum bayan kun gama min aiki ," Cikin tsananin murna da jin daɗi yakaka suke yi mata godiya kamar zasu kwanta mata ," su ai sun gama samun rufin asiri naira ɗari uku-uku a kullum me suka manta ? Cikin murmushin ƙeta take kallon su kafin ta ce su zauna a gefe za'a zo a fara gwada musu aiyukan su , A gaban idon su matan nan suka haɗa wutar nan suka juye rubabbar dawar nan cikin manyan yankakkun durum ɗin suna yi suna juya ƙwanƙwaso tare da bin kiɗan kalangun nan suna rere waka, tamkar dai ƴan matasan ƴan mata ba tsoffin matan da suka doshi shekaru sittin ba , ____ Bayan fiye da awanni uku da su yakaka suka ɗauka a wurin aikin su , zuwa lokacin dattijan matan nan larki da hema sun gama gwada musu duk aiyukan da zasu dunga yi kama tun daga kan shara da goge-gogen cikin shagon da ake sayar da tsattsamar giyar burkutun , da har kawo yanzu da ake aunawa su yakaka burkutun da zafin ta a cikin dogayen kofunan silver suna miƙawa ga mutanen da suke ta shiga da fita cikin maye da tamɓele , mata da maza , suna kuma karbar kuɗaɗen suna kaiwa duduwa wacce take matsayin mai tara kuɗin cinikin , su yakaka basu kai ga fahimtar burkutu giya bace domin basu san ta ba koh sunan ta ma basu taɓa ji ba, abun da suka fahimta kawai shine wannan abun da mutanen suke zuwa saya suke sha ,yana burkita mutanen tare da sanya su shiga wani mawuyacin hali na birkicewar tunani ," ta yadda zasu ga mutum.tsaf ya shigo wurin cikin nutsuwar sa amma daga zarar ya kurɓe wannan ruwan zazzafar burkutun kafin ya bar wurin zasu ga mutum ya fara surutai da layi wasu ma har da amai da faɗuwa," Wanda su da kan su a duk lokacin da larki ta buɗe murfin durum ɗin domin ɗebo ruwan burkutun , tururin sa da warin sa yana bugar da su ta yadda har suke jin kan su na juyawa ," koh sau ɗaya basu yi gigin ɗanɗana burkutun sun ji irin ɗanɗanon ta ba hasalima ma ita yakaka koh ruwa bata sha ba abincin ma da madam sally ta saya musu ita nata juye shi tayi a leda ta kulle da niyyar sai sun koma sansanin su suci ita da ƙanwar ta , yagana ce ta cinye nata ., Hankalin yakaka ya fara tashi ne lokacin da ta fara ganin hadari yana haɗuwa a garin , gashi kuma lokacin tashin su bai yi ba ," Zuciyar ta ta cika taf da tunani tare da zullumin halin da falmata take ciki , Allah-Allah take lokacin tashin nasu yayi ta tafi ga ƴar kanwar ta kafin ɓarkewar ruwan saman da ta san barazana ne ga lafiyar falmatan ," A karo na barkatai larki ta sake miƙawa yakaka dogayen kofunan da suke cike da barasa mai turiri , tare da umartar ta ta miƙa su ga mutanen da suka bada kuɗaɗen su yanzu , cikin rashin kuzari yakaka ta karbi kofunan tana mai ɗaga kan ta tana sake kallon ɓakin hadarin da ya shata layi a sama yake ta faman rugugi ," Dai-dai ta sanya kai cikin shagon taji wata irin ƙarar da ta razana ta sanya ba shiri ta saki kofunan dake hannun  ta suka tarwatse ruwan ciki ya watsu a jikin mutane biyun da suke zaune daga farkon shagon akan kujeru suna kurbar ruwan su ," Zafin kakkarfan marin da ya sauka akan kumatun ta shi yayi sanadiyyar dawowar ta cikin hankalin ta da ta rasa na ƴan daƙiƙu sakamakon ƙarar tashin bom ɗin ,"       Dan uban ubanki shegiya baki da hankali ne zaki ƙona mu ? Ƴar mahaukaciya ko yau kika fara jin irin ƙarar tashin bom ɗin nan kina maiduguri ? Bace mana anan kafin mu tattataka ki ƴar*    Kusan dukkanin rabin mutanen da suke cike cunkus a cikin shagon suka kwashe da wata irin mahaukaciyar dariya suna nuna ta , ita kuwa sai wuri-wuri da ido take sam zafin marin bai ɗimautata ba kamar kalmar bom da taji mutumin da ya mare tan ya ambata ," bom aina kuma bom ya tashi ? Falmata ita ce kalmar da ta fara tasowa ta daga ƙarƙashin zuciyar ta ta kuma bayyana kan ta akan laɓɓan ta ," Da gaggawa ta sunkuya ta tsince kofunan da suke ƙasan kunnuwan ta sun toshe daga barin jin dararrakin mutanen da suke wajen , ta juya cikin sassarfa ta koma ciki  ," A tsaye ta taradda yagana wacce itama alamun firgici yana bayyana baro-baro akan fuskar ta ,"basu samu damar magana ba sakamakon wayar da madam sally fara wacce take bullowa daga wani ɗan lungu a tsukin wurin da suke zaton gida ne ta cikin lungun , wayar da take yi ta ɗauki hankalin su ,"          Ni sally naga ta kaina bom a post-office ? Na shiga uku kadda dai yayi mummunar barna ? Tabdi Allah dai ya kwashewa waɗannan mutanen albarka tsinannun banza kana zaman zaman ka su aika da kai barzahu ," toh yaya zaka shigo ɗin ne ? Ga fa ruwan yana jiran ka kar ya huce ," ta karasa zancen ta tana sakin shewa tamkar ba ita ta gama bayyana jimami ƴanzu akan fuskar ta ba ,' Da sauri yakaka ta ƙarasa gaban madam sally ta durƙusa ," tare da sunkui da kan ta tayi shiru ," dukkan su idanu suka zuba mata suna sauraron ta , tare da kallon jikin kayan ta da burkutun ya jiƙa ,"     Ganin tayi shiru bata ce kome ba ya sa madam sally fara jaan wani guntun tsaki ,"       Ke ban son iskanci meye zaki wani zo ki tare min hanya kuma ki ƙi cewa kome, idan aikin ne baza ki iya ba ki faɗa min sai na baki iya kuɗin awanni da kika min ki kara gaba Da sauri yakaka ta ɗago kai jin ana shirin korar ta , cikin karkarwar murya da inda-inda tace ,"     Madam dan Allah ina ne inda naji ana cewa bom ya tashi ? Nan kurkusa ne ?       Kallon banza madam sally ta yi mata , kina nufin baki san post-office ba kina garin nan toh ta ina kuka zo ? Ku da kuka ce kuna camp ?  Inda mota ta biyo da ku daga camp zuwa cikin gari ta sauke ku nan ne post-office kusa da kasuwa monday market ," Zuruf yakaka ta miƙe tana rarraba ido  , da sauri kuma ta sake durƙusawa , madam dan Allah ƙanwata falmata , ƙanwata falmata tana bakin kasuwa tana bara , kuma bata san ko'ina ba makauniya ce ," dan Allah ki taimaka ki min izni naje na zo da ita ,"  ta karasa zancen ruwan hawaye yana sulluɓowa akan kududdukin ta ,"     Karo na farko madam sally taji ɗan tausayin yaran ya kama ta ,"       Babu kome kina iya tafiya ƴar uwar ki sai ta ƙarasa aikin tun da bai wuce awa ɗaya da rabi ba masu aikin dare su iso ,ungo kuɗin sallamar ki ,kiyi sauri kije kar a fara rurrufe hanya a hana wucewa ,' Kallon yagana tayi wacce ta so da madam sally ta bar su sun tafi tare kamar yadda suka zo , sai dai babu yadda zata yi ita ma alfarma aka yi mata domin duka aikin da suka yi bai wuce na awa uku ba ,"   Yagana zan tafi zamu jira ku a tasha .    Yakaka zaki iya gane hanyar fita daga unguwar nan ? Kar ki ɓata fa    Zan iya ganewa yagana sai kun zo ! Daga haka ta matsa ta ɗauki ledar da ta ƙulle abincin ta a ciki , cikin sassarfa ta sanya kafa tana barin wajen ba tare da ta koh tsaya ta wanke wurin da ruwan burkutun nan ya bata mata zani ba ,"burin ta kawai ta iske ƙanwar ta a inda ta bar ta cikin ƙoshin lafiya ,"     Zamiya da zilliya ta dunga yiwa kattin mazan da suka buge tatil da giya a cike da wannan filin da ake kaɗa kalangu ,suna ta rawar banza da fitsara sun kama ƙugun matan banza ,"tamkar dai basu da masaniyar halin tashin hankalin da garin yake ciki ," Bata bi ta kan kolo ba kawai ta ɗauki hanyar da suka biyo a yayin tohowar su tana tafe tana jefa kafa tare da share guntayen ƙwallar da suke silalowa lokaci-lokaci daga gurbin idanun ta , zuciyar ta cike taf da fargaba ta ƙagu ta isa wajen falmata ," Ji tayi kamar ana ɗan taɓa ledar hannun ta , cikin hanzari ta waiwayo ,"     Shiɗewar wucin gadi tayi lokacin da tayi ido huɗu da wata mayunwaciyar karya baka kirin da ita tana dalalo harshen ta waje , ƙamewa tayi ƙyam tana jan numfashi da ƙyar suka yi kallon kallo na kusan minti guda da bakar karyar nan ," kafin yakaka ta zabura tare da yankawa da gudu cikin matukar gigita da tsorata ,"  karyar nan kuwa bata bata lokaci ba gurin rufa mata baya ita ma a guje tana haushi ," Gudun fanfalaki yakaka take yi tana yi tana waiwayon karyar nan da zuwa yanzu suka zama su biyu ne suke bin ta tare da wani ƙaton kare ,"  Kutsawa take tsakanin layukan unguwar ba tare da tana lura da inda take bi ba , taimako take nema amma abun takaici duk da unguwar cike takd da mutane dattajai da matasa , cikin su babu wanda yayi yunkurin taimakon yakaka , sai ma dariya da ihun da matasan suke bin ta da shi har ta ƙulewa ganin su a guje , yara kuwa suma rufa masu baya suke yi da gudu suna ihu da dariya tare da kiran sunan kanukan suna tafi," Tahowa yake daga cikin siririn layin da baya bullewa , fuskar sa sam babu annuri da alama akwai abun da ke damun zuciyar sa ," Tun a nesa ya fara jiyo hayaniyar su kafin ya hango shawo kwanar da tayi a guje tana mai jefa kafar ta cikin dagwalon kwatami bayan ta karnuka biyu su ma a guje kafin ya ga bullowar zugar yaran da ya jiyo ihun su biye da ita," Gadan gadan ta nufo shi , yana yunkurin kauce mata , yaji ta taho gabaɗaya ta faɗa cikin kirjin sa tare da zagaye hannuwan ta tsam da jikin sa , dai-dai lokacin da karnukan ke karasowa .!   Masoya me kuke tunani?   me kuma zaku ce ? Yaya kuka ga shafin nan ? kar ku manta sharhin ku shine tukuici na , shi kuma zai bani karfin gwaiwar cigaba da sambaɗo muku hargitsin rayuwar ƴan matan uku #vote #comments #share #fikrh [6/24, 10:57 AM] +234 701 013 7848: Fikrah writers association MAFARI....... ( Hargitsin rayuwa ) 12 Cikin hanzari ya raba ta da cikin jikin sa ya sauya mata matsaya zuwa bayan sa lokaci guda ya sa kafa ya kaiwa bakin "karyar" duka ,a dai-dai lokacin da tayi nufin kaiwa ledar hannun yakaka wawura ,wanda hakan ya sa yakaka ta sake riƙe bayan rigar sa tamau tana me sake mannewa da jikin sa cikin karkarwa tare da runtse idanun ta ,batare da tayi la'akari da kyau gami da hasken lallausan yadin jikin sa ba , Ke dallah Sakar min riga koh bakya gani karnukan sun gudu ne ??      Cikin hanzari yakaka ta buɗe idanun ta da suke runtse tare da sakar mishi riga gami da matsawa daga jikin sa kunnuwanta suna jiye mata kamar ta san muryar sa . Ba tare da ya waiwayo ta ba ya cigaba da takun sa da nufin cigaba da tafiya inda ya nufa , Bayan sa ta bi da kallo bakin ta na son furta masa kalaman godiyar taimakon da yayi mata , idanun ta suka sauka a dai-dai inda ta kama a jikin rigar sa har zuwa ƙasa baki ɗaya ya baci da jar miyar da tasha gumurzu da karnai akan ta ," Zaro idanuwan ta tayi lokaci guda ta buɗe ƴar muryar ta ,"     Malam , malam Ta kira sa   Waiwayowa yayi yana me sake tamke fuskar sa ,    Karaf suka haɗa ido , kallon-kallo suka yi yayin da idanun su suka sarƙe cikin na juna a karo na biyu , Kowannen su zuciyar sa ta buga da mabanbanta yanayi.,"     Yakaka tayi saurin janye ƙwarar idanun ta lokaci guda mabayyanin bacin rai yana samun matsuguni akan ƴar fuskar ta a saboda hoton cin zarafin da yayi musu ita da kanwar ta da ya gifta ta cikin zuciyar ta a take ,"      Haɗiye kalaman godiya da ban hakurin bata masa riga da tayi niyyar yi tayi ,domin a ganin ta wannan mutumin bai dace da samun tattausan kalamai daga gare ta ba .   Cikin sauri ta taho kan ta a sunkuye ta kewaye shi , cikin dakewar zuciya ta sake nufar hanyar da ta billo daga kan ta ba tare da ta sake yadda ta dubi sashin da yake tsaye ba .   Tare da wani irin yanayi da yake ji daga ƙarƙashin zuciyar sa wanda ya kasa tantance wanne iri ne , ya bita da kallo , chan ƙasan zuciyar sa wani ƙaramin sashi yana mararin sake duban cikin ƙwarar idanun ta , wanda a zahiri bayan ƙwarar idanun nata da suke da wani irin maganaɗisu a gareshi babu wani abu da zai iya ɗorarwa na daga kammanni koh suffar yarinyar illa ma , ƙyama da haushin ta da yake ji tun a ranar da ya fara yin tozali da ita ,dan haka yanzu ma sashi mafi rinjaye na zuciyar sa danasanin taimakon ta da yayi yake , har ma yake kitsimawa cikin ransa da ace ya san ita ce da ya bar karnukan nan sun chasaa ta yadda ya kamata ,"bagidajiyar wofi ƴar ƙauye " ya karasa tunanin sa yana mai fidda sautin dogon tsaki ,"mtsww"    Cikin taka tsan-tsan tare da taraddadin sake gamuwar ta da rundunar karnuka take ratsa layukan da nufin komawa kan hanyar ta da ta biyo domin ta samu damar nufar wurin da ta bar falmata , sai dai abun da ya firgita ta shine bacewar da tayi ta gagara gane hanyar da ta biyo . Bulayi ta dunga yi ,ta bulla ta chan ta bullo ta nan gabakidaya kan ta ya juye ta samu makuwa , Cikin rishin kuka ta ɗaga kai tana kallon ruwan saman da ya fara sauka da matuƙar karfi , yayin da mutane kowa ya fara neman mafaka . Share hawayen ta tayi tana me ƙanƙame jikinta saboda dukan da ruwan ya fara yi mata , sake mikawa tayi ta nausa inda take tunanin zai sada ta da bakin hanya ,idanun ta koh gani sosai basa yi saboda ruwan hawaye da karfin ruwan saman da yake sauka bisa fuskar ta . Dai-daita tsayuwar motar sa yayi a gefen hanya saboda karfin ruwan da yayi yawa tare da ƙuncin da ya cika masa zuciya sun haɗu sun hana shi samun damar da zai jaa motar sa ya ƙarasa barin unguwar da yake ƙi fiye da kowanne bigire cikin duniya wanda kuma shigar sa unguwar ya zamar masa dole saboda dalili mai karfi . Baya yayi da kujerar motar bayan ya ƙarawa kan sa karfin na'urar sanyaya waje , ya kwantar da kan sa wanda yake sara masa akai-akai , Sake juya kan sa yayi ta ɗayan bangaren da yake kallon layukan cikin unguwar yana kallon yadda kakkarfan ruwan saman yake wanko dauɗa da tarkacen sharar cikin unguwar yana watso su cikin wata ƙatuwar ƙwatami da ta shata a bakin layin , Tsumu yayi ya ƙurawa kwatar ido yana tunanin da yake ƙara dagula masa sauran farin cikin sa , har zuwa lokacin da kwatamin ya cika ya tunbatsa ya shafe a ƙasa tare da dai-daituwa da sauran ruwan da ya cika unguwar kasancewar ta a cikin kwari , Tun a nesa ya hango ta ita ɗaya tal akan layin tana jaan kafafun ta da suke nutse cikin ruwan dattin da ya kawo har zuwa ƙwaurin ta , ta tukuikuye cikin yagalgalallen hijabin ta sai rawar sanyi take tana karkarwa , karfin iskar da ruwan saman ke tafe da shi suna barazanar yin wurgi da ita , Tsaki ya jaa a karo na barkatai a fili ya furta "mahaukaciya" juyar da kan sa yayi zuwa ɗayan bangaren yana me lumshe idanun sa ,"    Chan daga cikin kwakwalwar shi yake jin kamar ana umartar sa ," Cikin sauri ya buɗe idanun sa da suka yi jaa a sakamakon runtse su da yayi da kuma sara masa da kan sa yake ," cikin abun da yake ƙasa da minti guda ya buɗe murfin motar da matuƙar karfi gami da fita a guje ," Wani irin sura ta ji anyi mata tare da yin juyi da ita da ya sa leɗar abincin hannun ta ta subce gami da faɗawa cikin ruwan da yake kwaranya da gudu ya wuce da ledar . A tsorace ta ɗago kan ta bayan da taji an ɗire ta a gefe ,ta watsa matsakaitan idanun ta akan fuskar sa da ruwan sama yake tsare , Ke wacce irin daƙiƙiyar mahaukaciyar yarinya ce ne ? Cikin HARGITSIN nan sai yawo kike , ana ruwan sama ma baza ki samarwa kan ki mafaka ba ? Yanzu ba dan Allah ya sa na lura ba da kin je kin faɗa cikin kwatamin nan kin kashe kan ki a banza mahaukaciya ," ya karashe zancen yana mai jin kamar ya rufe ta da duka . Sarai ta fahimci ya zage ta saboda kalmar mahaukaciya da ya danganta ta da ita ,wacce cikin kalaman batanci da yayi amfani da su ita kaɗai ta gane ,' da hakan ya haɗu da asarar abincin da ta ci uwar wuya akan samun sa , da yanzu take ganin wannan mutumin da bata koh kai ga sanin sunan sa ba a matsayin wanda ya jawo mata asarar abincin yake kuma binta da zagi , bacin ran haka ya hana ta fahimci sauran kalaman sa dake bayyana mata irin hatsarin da ta shiga sai ma zuciyar ta da ta ɗau zafi da yayi sanadiyyar sake ballewar ruwan hawayen ta .    Kewaye shi tayi tana mai sake jin tsanar sa cikin ranta ta sake nufar hanyar ta , bata yi taku biyu ba ta ji an fisgo ta , kafin ta ankara ta ji saukar kakkarfan mari a kumatun ta na dama kafin ta samu daman wartsakewa ta ji an fisgi hannun ta . Bai sake ta ba sai da ya kawo ta jikin motar sa ya tura ta ta haɗu da jikin motar da karfi ,  bai bi ta kan ta ba ya zagaye ya buɗe motar ya shiga ya jaa kofar da karfi ya rufe tare da sake mayar da kan sa ya kwantar . A hankali ya fara jin sanyin da motar ta ɗauka tare da wanda garin ya ɗauka baki ɗaya a sakamakon tsagaituwar ruwan saman da wata sassanyar iska da take kaɗawa suka haɗu suka fara sashi jin matsanancin sanyin da ya sanya shi buɗe idanun sa  ya sauke akan bayan ta da take tsaye a inda ya hankaɗa ta koh ƙwakƙwaran motsi bata yi ba , Dauke kan sa yayi yana mai jin wani yanayi mai kama da matsanancin tausayi yana neman mamayar sa ," Ya yunkura gami da kai hannu ya kashe ac tare da kai hannu ya murɗa ɗan mukullin motar sa ," A firgice ta matsa daga jikin motar tayi baya tare da juyowa ta fuskanto motar tana mai sake takurewa saboda azabar sanyin da take ji ,"  Sai dai saɓanin ɗazu yanzu fuskar ta ta ɗan sake daga tsananin bacin ran da take nunawa hakan kuwa baya rasa nasaba da fahimtar da tayi cewa ya taimake ta ne , ya ceto ta daga hatsari  a saboda bayan ruwan ya fara tsagaitawa ne babbar kwatamin ta baƴyana , wanda hakan ya sa ta fahimci taimakon da ya sake yi mata a karo na biyu , Baya yayi da motar sa ya karya kan motar ya hau titi sosai , sai a lokacin ya kallo in da take suka haɗa ido ," Da sauri kowannen su ya ɗauke kan sa ya jaa motar da matukar karfi wanda hakan ya sa ruwan da ke kwance kan titin ya sake fallatsuwa mata a jikin ta ,.    Tsayuwa ta cigaba da yi tana mai fuskantar titin tare da jin wani sabon tashin hankalin rashin ganin alamun mutane a bakin titin da zuwa yanzu ta fahimci ta nan suka shigo unguwar sai dai lokacin da suka zo wurin cike yake ta ko'ina da jama'a tare da rumfunan saye da sayarwar su na wucin gadi , yanzu kuwa babu jama'ar babu rumfunan su hakan ya sa baza ma ta iya tantance dai-dai wurin da suka bar falmatan ba Da gudu ta tsallaka titin tayi diri-diri cikin rashin sanin takamaimai bangaren da zata nufa hagu koh dama , da sauri ta fara bin bangarenta na dama wanda ta nan suka bar falmatan sai da ta dangana har karshe ta je ta tarar da roundabout "shataletale" bata ga koh alamun falmatan ba , kai mutane ma tsilla tsilla take cin karo da su suma kuma duk hanya ɗaya suke bi , sai kuma tsirarun motocin da suke wucewa da gudu suna watsa mata ruwan kan titin , Dawowa da baya ta sake yi da nufin nufar bangaren hagu sai dai wannan karon ta sauya salon neman ,domin dagewa tayi tana buɗe murya tana kwalla kiran sunan falmata ,bata damu da kallon da tsirarun mutanen da take yin taho mugama da su suke yi mata ba , burin ta koh ita bata ga falmata ba falmatan ta ji muryar ta ta amsa mata ," Nasan kun gaji , nasan kun min uxuri ,nasan kun tsumaye ni , nasan ya kamata na baku yafi haka , toh amma yanayi ne ya zo da haka ,ina fatan zaku ƙara hakuri , kuyi fata daga yau babu sauran dogon jira , wanda nima nake fatan haka . Inaso mu shawarta zaku dunga hakurin ganin posting sau ɗaya koh biyu a sati amma da dogon jadawali mai ɗauke da kimanin kalmomi dubu takwas zuwa tara / koh kuwa zaku fi son gajeran jadawali a kullum ,mai ɗauke da kimanin kalmomi dubu ɗaya zuwa biyu ? ??? Ina jiran ra'ayoyin ku , yadda kuke so haka za'a yi insha Allah       #son so #fikrh #umm'muaz [6/24, 10:57 AM] +234 701 013 7848: Fikrah writers association. MAFARI ......... ( Hargitsin Rayuwa. ).... umm'muaz 13 Tuki Hamza yake cikin rashin kuzari wanda ba domin kan titin shal yake babu kowa ba a sakamakon gudun da kowa yayi  , da tabbas babu abunda zai hana ya samu tukuicin zagi daga wurin sauran direbobi saboda sam ya gaza yin sauri , zuciyar sa taƙi aminta da ya tafi ya bar ta cikin halin da take ciki , wani sashi na zuciyar na son sanin me ma ya kai ta wannan unguwar wacce take cike da hatsari .? Gangarawa yayi gefen titin ya tsaya dai-dai lokacin da tunanin abun da zai iya samun ta marar kyau idan har dare yayi mata a wannan unguwar ya gitta masa , da hakan ya sa ba shiri ya karya kan motar ya juya batare da la'akarin ba akan hannun da yakamata ya juya bane . Wannan shine karo na biyar da take safaa-da-marwaa a bakin babban titin tana mai kwalla kiran sunan falmata , wanda zuwa yanzu da ta kawo tsakiyar hanyar ta ji juya ya fara kwasar ta a sakamakon muguwar yunwa da kishirwa gami da tsantsar sanyin da yake ratsa bargo da kasusuwan ta ta jikin jiƙaƙkun kayan ta da iska ta fara busar da su , Ba shiri ta dira guwowin ta duk biyu a ƙasa tare da sake fashewa da wani matsanancin kukan da baya fitowa sosai a sakamakon kwalla kiran da take ya fara dusar da karfin muryar ta . Kuka take bilhakki tana kiran sunan falmatan a hankali cikin ƙaramar murya ," Falmata nyi dan3? ( falmata kina ina ?) Falmata nyi dan3? ( falmata kina ina ?) Allahgammama falmata are3 nyi baa maa range3 kindaa dikkin3 baa ," (Dan Allah falmata ki dawo idan babu ke bazan iya rayuwa ba ) Ƙarasa bajewa tayi daɓas a cikin guntun ruwan da yake wajen idanun ta na fara ganin bibbiyu , Daf da ita ta bayan ta ya zo yayi birki , kallon ta yayi ya ɗauke kai gami da matsa mata hon , Taji ƙarar motar sarai a daf da ita amma bata yi wani alamu na motsawa ba hasalima wani ɗan guntun tunani ne ya gifta mata na ina ma da motar nan zata take ta ta mutu ita ma kamar yadda mahaifin su ya mutu take kuma hasashen mahaifiyar su da sauran kannen ta ciki har da mafi soyuwa a gareta "falmata" duk sun riga sun mutu sun bar ta ," tunanin hakan da tayi ya sa ta sake muskuɗawa ta matsa kan titi sosai yadda zata bawa motar da ta taho damar bi ta kan ta ," Wani dogon tsaki ya saki ganin yadda ta rarrafo ta hau kan titi a maimakon ta taso ta zo su tafi kamar yadda yake nufi , Balle murfin motar yayi ya fito laɓɓan bakin sa suna furta kalmar "sokuwar banza ƴar kauye ", Tsayuwa yayi a kan ta ya zuba mata ido yana nazarin ta cikin tantamar samuwar cikakken hankali a gareta , gefe guda na zuciyar sa na yaba kyaun dogayen fararen yatsun kafafu da na hannayen ta da suke zara-zara kuma fasalin yatsun hannayen nata kamar an feƙe fansiri haka suke da ɗan tsini ta saman su , gwanin ɗaukar hankali duk da ɗauɗa da maikon miya da suka bata su . Tsayuwar sa akan ta bai sa ta ɗago kan ta da ta ɗora bisa hannayen ta dake kan guwaowin ta ba wanda hakan ya bata ɗamar dunkulewa guri guda tana jiran motar tayi awon gaba da ita ," Ganin taƙi ɗago kan nata ya sanya ransa sake ɗugunzuma ganin sa tana neman ɓata masa lokaci alhalin shi taimakon ta kawai yake son yi wanda har zuwa yanzu ya rasa dalilin da ya sa yake son taimaka mata ,"     Ke duba bana son wawanci ki taso na mayar da ke sansanin ku tun kafin dare yayi miki anan karnuka su yagalgala ki ,     Hamza ke furta hakan yana yi yana yamutsa fuska tamkar an sanya shi yin maganar a dole ," Har illa yau dai yakaka taƙi ɗago kan ta taƙi cewa koh uffan duk da cewa ta gane shi ,a ranta kuwa ta gama yankewa kan ta shawara a dalilin zancen karnai da ta ji ya ambata wanda take taji hanyar mutuwar ta mafi sauki shine kawai ta kwana a nan wurin domin tana da tabbacin idan har tayi ido biyu da karnuka a sulusin dare babu abun da zai hana jijiyoyin da ke kai jini cikin zuciyar ta su tsinke ta mutu nan take ," tunanin hakan ya sa ta sake gyara kwanciyar kan ta ta maida fuskar ta zuwa ɗayan bangaren cikin sallamawa.   Wanda hakan ya bawa hamza damar ganin fuskar ta da jijiyoyin kan ta daga goshin ta da na gefe-gefen idanun ta suka taso raɗa-raɗa koraye shar "kasancewar ta fara sol "   Firgita yayi da ganin ta a haka wanda a take ya fahimci rangwamen lafiya a gare ta kasancewar sa cikakken likita kuma kwararre wanda gwamnatin jaha ta amince da shi har ya zama ɗaya daga cikin likitocin da ke kula da marasa lafiyan dake sansanin ƴan gudun hijira . Sunkuyawa yayi a gaban ta gami da kai hannu ya taɓa goshin ta ," a ɗan tsorace ta ɗago da idanun ta da suka ƙanƙance gami da sake zurmawa ciki ainahin launin su na zaiba-zaiba kamar gilashi suka bayyana tar ," Da sauri ya janye idanun sa daga cikin nata sakamakon ji da yayi kamar akwai wani ɗigo dake sashi cikin wani yanayi tun daga ƙasan ruhin sa a tare da idanun yarinyar .   Ya janye hannun sa tare da miƙewa ya tsaya ,"     Baki da lafiya , ki taso mu tafi na mayar da ke sansanin ku a duba ki a baki magani zaman ki anan hatsari ne ,"    Kin ji koh ?     Jin ta sake yin shiru a karo na biyu ya sa shi shafa sumar kan sa cikin gundura da halin ta ,"gefe guda na ran shi yana mamakin kan sa ta yadda ya damu har yake rarrashin ƴar gudun hijirar da bai san ma daga wanne ƙauye take ba.    Ke idan baza ki tashi ba zan cicciɓe ki koh da bakya so na kai ki saboda hakki na ne na kula da lafiyar ku , ( haka kou ? naga alama 😂 )   Ji da tayi yace zai ɗauke ta ya sa ta miƙewa tsaye batare da ta bari sun sake haɗa ido ba , ta nufi cigaba da tafiya ,   Idan kika sake kika sake taku biyu da waɗannan ramammun siraran kafafun naki zan ɗaga ki sama na jefa ki cikin mota ,"idan ya so ki karye ma ke kika sani doluwa kawai , "dan ma kin samu ina sauke hakki na na taimakon ki da Allah ya ɗora min shine zaki dunga min iskanci da reni ,??? Tare da rashin jin dadi danganta ta da yayi da mai reni ta koma da baya ta tsaya a jikin motar ,' tana mai riƙe kan ta da hannu bibbiyu wanda yake masifar yi mata ciwo tamkar zai faɗo ,"   Da sauri ya buɗe mata murfin motar    Shiga muje ! ?   Tafiyar kurame ita ta biyo bayan gudun da hamza yake shararawa akan titunan da babu wani wadatar motoci , cikin mintuna goma sha biyu ya karaso bakin sansanin nasu ,"      Sauke gilashin motar yayi gami da gaisawa da sojojin da suke gadin sansanin da hakan ya sanya yakaka ɗago kan ta da tun da ta shiga cikin motar yake sunkuye ," Karaf ta sauke kwarar idanun ta akan ta tana tsugunne a tsakiya tana fuskantar duk wanda zai shigo sansanin ,"daga inda take tana hango yadda take rawar sanyi da jikakkun kayan jikin ta ," Wani irin numfashi ta sauke mai tafe da nishin jin daɗi bata yi wani jinkiri ba ta fara tura murfin kofar da kokarin ɓalla ta ta fita ,'cikin sautin da yake bayyana tsantsar murna da farin cikin ta take jera kiran sunan ƙanwar ta ta ,"     Falmata nah !     Falmata nah ! Mayar da duban sa yayi inda yaga idanun ta suna kallo ,' yamutsa fuska yayi tamakar ya ga kashi ,"domin haushin yakaka da yake ji kaɗan ne akan irin tsanar da yayi wa falmata. Ke dallah ki nutsu kar ki ballamin murfin mota ," ke da baki da lafiya ina zaki fita da gudu ki je ?? Tun kafin ya rufe baki ta amsa masa cikin siririyar muryar ta da take gauraye da sautin farin cikin da ya gaza boyuwa har akan siririyar fuskar ta da siraran laɓɓan ta suke ɗauke da dariyar da har ya bayyana gajejjerun hakoran ta irin na ƴar uwar ta ,"    Na warke wallahi na warke falmata na ashe ta dawo bata mutu ba ,"bata ɓata ba dan Allah ka buɗe min kofa naje wajen ta wallahi na daina jin kowwane ciwo a jikina . Shagala yayi wurin sauraran sassanyar muryar ta da koh kaɗan bata tare da hayaniya uwa uba ɗan bakin ta da yake bayyana baki sidik ɗin dasashin ta da ya kawatu kwarai akan farar fuskar ta ," Jijjiga kofar tayi da ɗan karfi cikin nuna alamun ƙosawa     Dan Allah ka buɗe min ! Cikin sanyi jiki da sabon yanayin da yake ji yana ratsa kowanne sashi na zuciyar sa ya miƙa hannu a kasalance ya matsa ɗan mubuɗin kofar ta bude , fit ta fita a guje har tana koƙarin faɗuwa ," Takun gudun kafafun ta shi ya fara isowa ga kunnuwan ta kafin taji sautin muryar ta ," Zuruf ta miƙe tsaye ita ma tana ambaton sunan ta ," tare da nufar inda take jiyo tahowar ta ,"   Kyakyawar runguma suka yi wa juna zuciyoyin su suna masu cika da farin cikin ganin junan su cikin koshin lafiya bayan taraddadi tare da zullumin da kowaccen su ta shiga na tunanin rasa ƴar uwar ta ," Hannu bibbiyu yakaka ta tallafo fuskar falmata ," da take dariya Falmata ya akayi kika dawo ? Waye ya dawo da ke ? Meyasa baki jira ni ba a wurin kamar yadda muka yi yarjejeniya?  falmata kin tayar min da hankali dan Allah nan gaba kar ki sake tafiya wani waje mai nisa ki barni ,"     Yakaka nima ba'a son raina na matsa daga gurin da kuka ajiyeni ba , bom ne ya tashi yakaka , duk mutane suka dunga gudu ," kowa yana neman wajen tsira ," na rasa yadda zan yi , inaso naje inda kuke ban san wajen ba kuma bani da ido bare nima na gudu , Allah ne ya taimaka min , wannan mutumin da kuka ajiye ni a gefen rumfar sa shi ya kama hannu na ya kawo ni tasha , da nufin mu nemi ƴan uwa na tun da na gaya masa kuna kurkusa da wajen ya san za ku zo tasha ," sai dai wajen minti talatin babu wanda ya zo daga cikin ku ga gaf ake da fara ruwa , har ya yanke shawarar zai tafi da ni gidan sa , sai naji muryar "Kolo" tana kiran suna na  ,  nayi murna sosai domin a tsorace nake ina ta kuka ,"   Na tambayi kolo ina kuke ke da yagana ta tabbatar min da kuna tare kuma zaku dawo ," sai dai hankali na bai kwanta ba tun da muka dawo na kasa zama ina tsoron kar ku ɓata yakaka ku kasa gane sansanin mu ,"zuciya ta baza ta jure rashin ki ba yakaka ", domin bani da kowa bayan Alllah sai ke yakaka ," ta ƙarashe zancen ta tana mai kai hannunwan ta ta ɗaura akan na yakakan da take tallafe da kumatun ta ta zubawa ƴar kewayayyiyar fuskar kanwar ta ta idanu," kamar yadda fararen idanun kanwar ta ta ma suke fes akan fuskar ta tamkar dai tana kallon ta ," Murmushi tayi tana mai sake jin yadda zuciyar ta take narkewa da ƙaunar ƙanwar ta ,gefe guda tana sake jin zuciyar ta tana ƙarfi da ɗaukar ƙudirin zamantowa GARKUWA ga falmata ..!! ******** Kai kawo yake yi a gaban gungun zaratan sojojin cikin matsancin bacin rai yake magana da maɗaukakiyar murya ,"      Matsayin mu na jami'an tsaro ba shi ne zai bamu damar cin zarafin Al'umma tare da mayar da rayukan su ba a bakin kome ba ," ba'a bamu kaki da makamai domin naɗa mu jagorancin zalinci ga fararen hula ba ," sai domin mu basu kariya da tsaro tare da kwato musu hakkokin su ," sai dai yadda kuka tafiyar da mutanen ƙaramin ƙauyen da yake tsakanin yankin difa da birnin maiduguri ya sha banban da rantsuwar kare martabar jama'ah da muka yi ," labari  ya zo min na yadda kuka ci zarafin mutanen ƙauyen ta hanyar yi musu kisan kiyashi ƙona dukiyoyin su da yi wa matan su fyaɗe dan kawai an sanar da mu akwai ƴan tawayen boko haram daga cikin su , ni a matsayina na shugaban rundunar ku ba haka na tura ku kuyi ba ,"gwamnati ba mutanen ƙasa ta turo mu mu yaka ba face ƴan tawayen boko haram , ɗan tsagaitawa yayi yana mayar da numfashi ," Wannan ya zama karo na farko kuma na karshe da zaku hau kan mutanen gari da kisa a zuwan kuna yakar ƴan tawayen boko haram . Jaan kafafu suka yi suka buɗa gami da ƙamewa su sara masa da hakan yake nuni da sun karbi umarnin sa ," Shigewa yayi cikin ɗaya daga cikin manyan tantunan da suke kakkafe a sararin faffaɗan filin da yake cikin daji sosai daga gefen birnin na maiduguri . Zama yayi a bakin ƙatuwar katifar da take yashe cikin tantin gami da kama kan sa da hannu biyu , wani iri yake jin kan nasa yayi masa matuƙar nawi kamar ba nasa ba , ga zuciyar sa da tayi wani irin cunkushewa sam sam ba ya jin sa dai-dai da ya riga ya danganta abubuwan da yake ji da rashin shan abar sa "Burkutu" har na tsawon kwanaki biyu yau ana yinin na uku , Miƙewa yayi ya nufi wurin da jakankunan sa ke jibge ya jawo ɗaya daga cikin su gami da buɗe ta sai ga tarin kwalaben giya sumfuri daban daban da yayi guzurin su, ɗaukar ɗaya daga cikin kwalbaben yayi ya riƙe a hannun sa yana jujjuya ta ," Kwarai yana da bukatar son ya sha giya sai dai shi sam ba giyar ba turawa yake sha ba , hasalima idan ya shs giyar turawa bikita masa jiki take yayi ta haraswa tare da matsanancin ciwon kai ," giyar gargajiya ta burkutu ita ce abar shan sa . Mayar da kwalbar giyar yayi cikin sauran ƴan uwan ta gami da rufe jakar yana me miƙewa cikin ransa yana jin ya zama dole ya nemo burkutu duk inda take idan har yana so ya iya cigaba da rayuwa cikin kwanciyar hankali ya kuma gabatar da aikin da ya zo yi cikin nasara , tabbas burkutu ta zama mahaɗin rayuwar sa domin ji yake kamar zai iya rasa ran sa idan ya ƙara wasu awanni bai zubawa cikin sa ruwan zafin burkutun ba ," Da sauri ya fita daga tantin yana jin yadda kan sa yake jujjuyawa ," a take sojojin dake da alhakin kula da shi , kama daga tuƙa shi idan zai fita da masu rakiyar sa ,zuwa masu yi masa wanki da girki da sauran aikace aikace duk suka taso ," dakatar da su yayi ya kira direban sa kawai tare da yi masa umarnin ya tuƙa sa zuwa cikin birnin maiduguri ," . Lol 😂😂 Anya ma na kai 3k words ??? Aradu ban kai ba 😂 Well amma ai nayi koƙari koh ?? Alright naga ra'ayoyin ku kuma naji daɗin su sai dai kun sani fah akwai tarin aiyuka akan mu koh ?? Ok zaku cigaba da ji na akai-akai kamar yadda na Alƙwaranta muku insha Allah ," Kar ku manta da danna ɗan tauraron nuna yabawa , tare kuma da faɗin ra'ayoyin ku domin bani karfin guiwar cigaba da rubuto muku . #fikrh #umm'muaz [6/24, 10:57 AM] +234 701 013 7848: MAFARI ......        ( Hargitsin Rayuwa ) 14 umm'muaz Babban Barikin soja dake tsakiyar birnin maiduguri nan direban youssouf ya dakata , Karo na uku biyamuradi youssouf yana yunkurin faɗawa takwaran aikin sa kuma sabon aboki agare shi wanda ya kasance babban sojan nigeria mai matsayi irin na biyamuradi ( colonel ) amma sai ya ji ya kasa , saboda shi da kan sa yana jin kunyar mummunar ɗabi'ar sa duk da cewa kusan hakan ba bakon abu bane wurin su soji , amma yadda yake da kamala da nutsuwa a zahiri ,uwa uba kasantuwar sa ɗan nasaba da akan san su da kyaun tarbiyyah , tashin farko zai yi wuya ayi hasashen yana kurɓar burkutu ," Sake ƙutawa yayi a karo na barkatai yana me jin duk ya gundura da hirarrakin da abokin nasa mai suna "colonel nuhu " yake yi masa , ya kai ɗan yatsan sa ɗaya gami da sosa ƙeyar sa . Taɓo sa nuhu yayi lokacin da ya lura baki ɗaya youssouf ɗin bai bashi amsar hirar da yake yi masa tamkar ma hankalin sa bai tare da shi yayi zurfi cikin tunani .    Abokina yaya dai ?    Meye yake damun ka haka da har ka zurfafa cikin tunani ? Ɗan ƙaramin tsaki youssouf ɗin yayi kafin ya ce Bari kawai abokina akwai abun da nake bukata ne , Wani shu'umin murmushi nuhu yayi domin shi tun tuni ya harbo jirgin youssouf ɗin duba da yadda duk yake a birkice ga fuskar sa da take bayyana matsanancin halin da yake ciki ," amma dan ya sake tabbatarwa tare da son ya tsokani youssouf ɗin ganin kamar yana son boye masa cikin sa , ba tare da ya san shi da shi dukkanin su ƙwaryar sama da ta ƙasa ne ( duk kanwar jaa ce ) Me kake bukata haka abokina ?? Ɗago kan sa yayi da yake a sunkuye ya wara idanun sa da suka sauya launi zuwa jaa yana jin yadda nawin da ya tokare shi a kirji akan rashin samun kurbar burkutun yana sake ƙaruwa ta yadda yake jin tamkar matse masa jikin sa ake da dukkanin hanyoƴin jinin sa ," cikin wata irin sarƙaƙƙiyar murya yace ,"    Burkutu ," Burkutu zan sha nuhu ,' dan Allah ka taimaka ka kaini inda zan samu burkut da farko , zan yi maka bayani daga baya ,"  Wata shu'umar dariya nuhu ya kwashe da ita ,' haba abokina ai ba ma sai ka min wani bayani daga baya ba duk su biyun za'a tanadar maka a lokaci guda , kaga daga ka gama kora ruwa sai kuma a faɗa harka ," Shi dai biyamuradi youssouf bai ce kome ba hasalima bai kai gano ba cikin kalaman nuhu illah kawai ya ji ya fara samun nutsuwa tun da nuhu ya ce zai samar masa da abun da yake muradi ," Direban sa yayi niyyar kira amma sai youssouf ɗin ya dakatar da shi tare da faɗa masa shi yana bukatar sirri ne dan haka so yake su tafi su biyu kawai ', a cikin ran sa yana ƙudurtawa zai sanya ido sosai ya gane hanyar domin duk lokacin da ya bukata kawai ya tafi shi ɗaya ya shaa abar sa ba tare da rakiyar kowa ba , ba kuma tare da kowa ya sani ba. ( mai kowa me kome ya sani kuma yana ganin ka youssouf amm ) Haka suka kama hanya tare nuhu shi ke jaan motar suka keto titi tare da bullowa ta bayan kasuwa suka gangara zuwa cikin unguwar BULABURIN wacce kaf cikin garin anan kaɗai ake iya samun giyar gargajiya gangariya ƴar asali ," Suna yin fakin a harabar wurin da ya cika ya tumbatsa da mutane zuwa ababen hawan su sakamakon yamma da tayi ," kiɗa yana tashi ta cikin manyan sifikokin da suke a kusurwa huɗu na zagayen filin ,ga matan banza da shigar fitsara burjik suna kai kawo cikin sigar tafiyar tallata baiwar jikin su , kowacce taci bilicin tare da izgar doki a tume a kan ta yayi tozo kamar na tsohon rakumi ," Juyowa nuhu yayi tare da kallon youssouf da ya lura yana ƙarewa matan wurin kallo , cikin yanayin da shi nuhu bai kai ga fahimta ba ,"amma sai ya fassara kallon da na tsantsar zalama da nuna muradi ," Abokina duba waɗannan ba irin naka bane waɗannan duk ajawos ne na kananan yara ," daina ma kallon su irin naka suna daga ciki a adane ba kowa ke hayar su ba sai ire-iren mu manyan yara ," Yana kammala faɗin hakan bai jira cewar youssouf ɗin ba ya balle murfin motar gami da fita , Kutsa nan bulla ta chan suka bullo ainahin wurin da ake sayar da  burkutun da mashayan ta suka tabbatar da tafi ta ko'ina inganci a cikin da'irar wajen watau ( burkutun madam saly ) Suna doso wurin youssouf ya shaƙi ƙaƙƙarfan warin burkutun ya lumshe idanu yana sake jin nutsuwa tare da matsuwar ya ji ya kwankwaɗa , dan haka ya sake sauri ,inda suka tadda mutane akan kujeru gaban tebura , Ɗaya daga cikin ƴan matan wajen da suke da alhakin rabawar ga masu saya wacce take raƙube a gefe ita ce ta zaburo ta nufo wurin su ,' Tun da ta nufo su nuhu yake mata kallon sheƙeƙe , saboda sam ba ita yayi zato ba , ba kuma ita ya so gani ba ," budurwar sa ko kuwa ace farkar sa samy baby , yarinyar da take tashe a da'irar ta su ita yake son ganin kamar yadda ta saba taryar sa kaf ƴan matan wurin sun san shi kwastoman samy baby ne , saɓanin ta sai yaga wata yagwalgwalalliyar ƴar yarinya tana tahowa gare su hasalima shi tun da yake zuwa rumfar madam saly bai taɓa ganin wannan ƴar ƙwailar ba ," Da zuwan yakaka wurin ta ɗan rage tsawo tare da tambayar su kofi nawa zata kawo musu ," ɗauke kai nuhu yayi yana wani hura hanci domin shi gaba ɗaya ma ransa ya gama baci ," Biyamuradi youssouf da yayi baya da jikin sa akan kujera tare da yin ƙasa-ƙasa da idon sa tamkar dai yana gudun wani ya gan shi a wurin ",alhalin nan kuwa shauƙin burkutun ne ke kwasar sa da kamshin ta suka haɗu suka samar mishi da mutuwar jiki ," shine ya amsa mata cikin hausar shi ta bamarɗe ,"   " Ki ɓido min mai auki kawai " Kasaƙe yayaka tayi a tsaye cikin rashin fahimtar abun da ya faɗi ," hasalima hausar da ake yi cikin maiduguri ma da bata da nisa ba gane ta take yi sosai ba bare fa wannan gangariyar hausar sam bata tsinci koh kalma guda ba ," Sake rusunawa tayi tana me sake maimaita tambayar da tayi masu cikin gurbatatciyar hausar ta ,"   Wannan karon nuhu ne ya amsa mata a fusace ,'ke dallah cewa aka yi ki kawo dayawa ," Sum-sum yakaka ta juya da nufin zuwa ta kawo musu, 'conole youssouf ya bi takun kafafun ta da kallo yana saƙe ƙagauta," " dai-dai tahowar samy baby wacce shigowar ta kenan wurin aka yi dace idanun ta suka sauka kan yakaka tana abun da ta ayyana shi a taɗi da gwarzon ta na wannnan wattanni "conole nuhu" wanda a yanzu kaf samarin ta babu kamar shi a kuɗi da shi take tinƙaho ," A take wutar kishi ta ruru a ƙarƙashin ran ta ," wata irin bangaza tayi wa kafaɗun yakaka tare da sanya tsinin dogon takalmin kafar ta ,  ta take mata kan yatsun ta biyu tare da tsayuwa akan yatsun kafar sannan cikin raɗa bayan ta kawo bakin ta kusa da kunnuwan yakakan wacce ta ɗimauce cikin jin azabar takun da samy baby tayi mata tace ," yarinya ki kiyaye wannan ɗan itacen marmari  nane zan iya kashe wacce ta shiga gona ta har tayi gigin taɓa ɗan itaciya ta ,' Duk tsayuwar samy baby akan ƙafar yakaka biyamuradi youssouf yana ankare da hakan saboda idanun sa da suke wurin daman ," ji yayi tausayin wacce aka takewa kafar ya ɗan kama shi wanda tun daga kan kafafun nasu ya fahimci banbancin da ke tsakanin su ,ganin kafar yakakan duk dadbare-dadbaren datti ,ga manyan tsagun faso da datti ya samu mazauni na dindin-din wanda idan aka kwatanta da kafar samy baby da take a wanke a goge sumul-sumul tashin farko za'a fahimci baiwa ce da uwargijiyar ta , dan haka yayi tunanin yakakan wani laifi tayi wa samy take hukuntata ," sai dai duk da haka yaji haushin samy saboda shi mutum ne wanda sam baya son zalinci ," take yaji ya tsane ta , Ɗago idanun sa yayi ya sauke su akan fuskar samy baby wacce idanun ta da hankalin ta baki ɗaya yake kan "ɗan itaciyar ta nuhu "😁 da sauri yakakan ta wuce lokacin da ta ji samy ta janye kafar ta tare da yin gaba ,"  Kichibis tayi da madam saly wacce ta sawo kai kallon ta sama da ƙasa madam.saly ta jefa mata," yanzu yaks dan ubanki ban baki kayayyaki nace ki daina yawo cikin waɗannan shegun tsunmokaran ba , ace tsawon sati kenan yau da kuka fara zuwa min nan amma shegu ƙazaman banza kullum da daƙalkalallun kaya ɗaya? Kalen ku dunga sa min kostomomi amai ? Kuna yawo yarkace yarkace uwa sabbin  mahaukata ? A haka waye zai karbi abun hannun ki ya shaa ? Aaa ah ku ji min shegiyar yarinya zata min kashin kasuwa ta janyo min hasara ? Toh dan uwarki wuce maza ki je ki sauya kayan nan kamar yadda ƴar uwar ki ta sauya nata ,'idan ba haka ba a bakin aikin ki kin ji ko baki ji ba ? Da sauri yakaka take gyaɗa kai daga inda take rakaɓe ," Sake ɗaga kayan yakaka take tana jujjuya su tare da ɗora su a jikin ta tana gwada tsawon rigar wacce take ƴar ɗigil da kaɗan zata rufe mata cibiyar ta da ƴan guntayen hannu maƙale hammata , tare da ɗan siririn siket ɗin da ya shaa tsagu a gefe da gefen sa har fiye da rabin tsawon siket ɗin , Niyyar ta ta kaiwa falmata a ɗinke mata wuraren da suka yayyage a tunanin ta ," sakamakon ganin kayan ƙanana ne tunanin ta sun ɗangale mata ,  dan haka ta yanke shawarar kaiwa ƙanwar ta ," duk da tayi tunanin kayan zasu matse falmata kasantuwar ta ɗan fi ta kaurin jiki ," gefe guda na zuciyar ta tana jin zata fi samun farin ciki idan falmata ta samu sauyin sutura fiye da karan kan ta ," Zabura tayi tare da fara kokarin zare kayan jikin ta sauya , jin motsi da tayi yana nufo ɗakin da yake zaman mallakin ƴan aikin madam saly a nan masu kwana a gidan suke kwana su kuma da suke yini su tafi anan suke cin abincin su , ita da yagana da suke duddungura sallalolin su suyi sallah a ɗakin ," domin bayan su babu wacce ta damu da sallah cikin sauran ma'aikatan manyan su da yaran su da tsoffin su ," Juyowa tayi bayan ta sanya rigar a zaton ta madam saly ce ta leƙo ta ga koh ta shirya ," Karaf suka haɗa ido da ɗanliti wanda ya ɗaga labulen bayan ya tokare hannayen sa da jikin kofar yana ƙare mata kallo da jajayen idanun sa da suke cikin maye ," A firgice yakaka ta rarumi chukuikuyayyen hijabin ta ta suturta jikin ta ", tsaki ɗanliti ya jaa tare da ƙarasa shigowa ɗakin .,'    Aikin banza da wofi toh yarinya meye zaki boye min iyee ? Baya koh gaba ?? Baya dai kin san nima ina da shi , gaban ma idan naƴi niyya zan taso su ehe ,"     Jin tayi shiru ya sa ɗanliti buga tsaki dai-dai lokacin da yake zama a gefen wata yamutsatsiyar tsohuwar katifar da take yashe cikin babban ɗakin ,"     Ƙwaila ma irin ki me zan gani a wannan busasshen jikin naki da bana zaton koh nonon kirki kina da shi ," duk abun da zan gani na riga na gani a jikin jigajigan manyan mata ƴan uwana ," ya ƙarashe zance yana wani jijjiga da girgiza gwangonin kirjin sa da yake a bushe ƙaranbau," Raɓar jikin bangon yakaka tayi bayan ta sunkuya ta ɗauki tsohuwar rigar ta da sabon siket ɗin , ta suɗaɗa ta fice a ɗakin tare da nufar bayan gida domin ta sa siket ɗin ," Bayan ta ya bi da kallo ,"    Wai sunan wata kalma", Luwai ," yau naga ƴar kauye da lafiyayyar farar fata luwai-luwai,"ji yadda fatar ta take sheƙi da wani ɗan uban su fari na ainahi babu algus irin na su madam saly ," yarinyar nan idan ta samu hutu tabbas zata jaa gayu ahaayyee ,"gwara da babu ni a harkar ƴan maza ai da ganin da nayi wa bayan yarinyar nan da ace ina harkar maza da yau babu zaman lafiya,." Da raɓe-raɓe ta fito daga banɗakin tana tafe tana sake sauke siket ɗin ƙasa-kasa sakamakon tsagun sa da yake har ya zarta gwuiwar ta , Wurin karɓar burkutun suka haɗu ita da yagana da tun safe madam saly ta sata gyara mata cikin ɗakin ta ,"amma tsabar shirgin da yake cikin ɗakin bata samu damar kammala gyaran ba sai yanzu ," Kallon kallo suka yi da ita da yagana wacce ita ma take tsuke cikin sabuwar shigar da madam saly ta bata na wani chasasshen wondon jins da yake a ɓarƙe ta wurin cinyoyin sa da wata ƴar ɗangalalliyar riga mai siririn hannu ," fuskar yagana ta kalla kawai ta fahimci ita ma tirsasa ta madam saly tayi ,ta sa ta sanya kayan a dole kamar yadda tayi mata ," Ba wacce tace ga ƴar uwar ta ƙala suka ƙarbi manyan farantan silver da larki da hema suka ciccika musu ruwan burkutu a kofuna tare da jerawa akan farantan ," Tana shigowa ƴar rumfar ta doshi gurin da ɗazu wasu mutane biyu suka bukaci ta kawo musu burkutun dayawa ," Turus ta yi lokacin da ta tadda kujerun da ta bar su akai wayam babu kowa ," Ɗan waiwayawa tayi tana dube-duben wurin da zata hango su ,ga zaton ta kou sun sauya waje ne ," Sai dai jajayen idanun mazan da taci karo da su suna kallon ta ya sa nan take ta diririce saura kiris ta saki farantin hannun ta ,"fiye da rabin maxan wurin kallon farar doguwar yarinyar da take sanye cikin jaan yadin da ya sake fidda kyau tare da hasken fatar ta suke," giyar da suka shaa suka yi tatil tana sake ƙawata musu tare da girmama musu sassan halittar jikin ta daga yar ƙanƙanuwar yarinya zuwa cikakkiyar babbar budurwa ," nan take suka fara kawo mata wawura da chafka cikin tamɓelen su na mashaya,"  Zilliya da zamiya ta haɗa Allah ya bata ikon tsalleke farmaƙin da suke kawo mata , " dan haka gudu-gudu ta maida tiren burkutun tare da shaida wa larki, masu neman burkutun sun tafi . Ganin lokacin tashin su ya riga yayi "karfe biyar tayi " ya sa ita da yagana suka nufi ainahin cikin gidan inda anan ɗaki da falo gami da banɗakin madam saly yake ," Suna isa kamar kullum iwar haka suka tadda cikin falon nata a cike da manyan ƴan matan da suke ji da kan su ire-iren su samy baby ," sai karta suke da cha-cha suna yi suna haɗiyar ƙwayoyi tare da kora ruwan maganin mura da yake mahaɗin ƙwayar da suke sha ," Madam saly tana daga gefe zaune tsakanin wasu manyan Alhazawa biyu da alama wata magana mai muhimmanci suke yi ," Ɗan rakuɓewa suka yi daga bakin kofar a durkushe sannan suka sanar da madam saly lokacin tafiyar su gida yayi ,"   Kallon hadarin kaji madam saly ta watsa musu kafin ta balbale su da masifar basa ganin tana tare da baƙi ne ? Su waɗanne irin wawaye ne ? Hakuri suka bata tare da cigaba da tsugunno nan bakin kofar suna jiran ta ta kammala da bakin nata ," Sai da aka kwashe fiye da mintuna arba'in har duhu ya ɗan fara shigowa karfe shidda ta gabato , zuwa lokacin kuwa har kafafuwan su sun sage duk sun muzanta tsabar gajiya .," Sai da suka kammala maganganun da su basa iya jin me suke faɗi daga inda suke a sakamakon hayaniyar da take sake cika illahirin da'irar wajen ," basu ankara ba suka ji ta watso musu kuɗin aikin nasu ,"   Ga shi nan ,' ku tabbatar gobe kun zo akan lokaci sannan ku tabbatar baku dawo min nan wajen da waɗannan shegun tsunmokaran kayan naku ba ,"  idan kuwa kuka yadda kuka doso min nan wajen da wannan shigar taku uwa masu kwana akan bola toh kuwa a bakin aikin ku ," ni bana son ƙazanta ,"ta karashe zancen tana jawo wata jakar bagco ta tura musu a gaban su ," ga kaya nan kowaccen ku shiga bibbiyu da su nake so na dunga ganin ku ," kun ji koh baku ji ba ???   Cikin sauri su ka amsa da toh ! Sauri-sauri suka haura tudu tare da barin unguwar suka tadda falmata wacce har ta fara gundura da jiran su tare da fara jin tsoron rashin dawowar su har zuwa yanzu da take jin hayaniya ta ragu a bakin kasuwar alamar an watse domin tun ɗazu baba modu ,"mutumin da take zama a gefen rumfar sa ," ya tattara kayan sa tare da sauke rumfar ta sa yayi mata sallama ya wuce gida ," Ajiyar zuciya ta saki a take fuskar ta ta yalwatu da murmushi sakamakon jin muryoyin su yakaka ,"    Yakaka yau kun daɗe a wajen aikin da fatan dai lafiya ? Dan har na fara tsorata . Kamo hannun ta yakaka tayi tare da sarƙafe yatsun su cikin na juna,   Lafiya lau falmata uwarɗakin mu ce yau tayi baƙi shiyasa bata sallame mu ba da wuri , kin ci abincin rana dai koh falmata ?   Naci gƴaɗar naira ashirin yakaka ," ta furta hakan tare da miƙa mata ɗaurin bakar leɗar da take tara kuɗin barar ta a ciki  ,"     Wannan karon yagana ce tace ,"    Gyaɗar naira ashirin ba abinci bace falmata ina ma laifin ki sayi koh ƴar awarar hamsin ,"ki daina zama da yunwa kullum muna faɗa miki ,ai yunwa tana daga cikin dalilin da yasa muka fito nema , toh me yasa zaki sake zama tare da yunwar bayan kuma akwai kuɗin sayan abincin a tare da ke ,"    Shiru falmata tayi ba tare da tace ƙala ba cikin ran ta kuwa tana sake kuɗurce niyyar cigaba da tara kuɗin barar ta , har sai ta samarwa da yakaka iya adadin kuɗin da zai isa ta jaa jarin kowacce irin ƙaramar sana'a ce da zasu iya dogara da ita ba tare da yakaka taje tayi aikatau ba ," Yakaka kuwa da ita ma bata ce kome ɗin ba idanun ta ne yake bisa kan wata mata da take soya doya da kwai daga gefen bakin tashar ," sakin hannun falmatan tayi ba tare da ta amsa tambayar da falmatan take yi mata ba na "ina zata" ? Ta nufi me sayar da doyar , ta miƙa naira ɗari daga cikin kuɗin aikin ta ɗari uku ,"ta ce a bata doya ," Kamo hannun falmatan tayi tare da zaunar da ita akan wani ɗan fasasshen buluk ta tsugunna ta buɗe ledar doyar tare da ɗaukar yanka ɗaya ta nufi bakin ta da shi ,"buɗe bakin ki kici zaman ki tare da yunwa barazana ce ga kwanciyar hankalina falmata , babu amfanin wuni da nake ina aikayau idan har ke zaki wuni tare da yunwa , alhalin kina zaune a bakin hanya cikin rana kina bara , na kasa baki kulawar da ta dace , rashin amfanina zai yawaita a gare ki falmata idan har ya zama na kara miki da yunwa daga yau kar ki sake zama da yunwa duk kuɗin da aka baki na sadaka ki daina ajiye ko sisi duk ki sayi abinci ki ci , ki  ƙara girma ki zama ƙatuwa ko bakya so idan mama ta gan ki ta ji daɗi tare da yaba min akan na kular mata da falmata mafi soyuwa agare ta cikin ƴaƴa ??", Tun da ta fara maganar take taunar doyar da ta sanya mata cikin baki tana murmushi , kammala maganar ta ya zo dai-dai da fitowar ƴar siririyar dariyar da tayi jin an ambaci kalma mafi daɗin sauraro agare ta watau " dawowar mahaifiyar su"      Nagode yakaka a kullum ina alfahari da yawan ƙaunar ki gareni ina kuma rokon Allah nima ya bani damar da zan nuna miki kulawa koh da bata kai yawan wacce kike min ba ,Allah ya bayyana mana mama tare da su baana cikin ƙoshin lafiya ,"   Su duka suka amsa da ameen har yagana da take kallon su cikin sha'awar yawan kaunar da suke yiwa junan su ," A gijiye likis suka dawo sansanin nasu amma hakan bai sa ,"fanna da ajus sun tsahirta musu ba domin tamkar jira suke su sanyo kafafun su cikin camp ɗin su tare su da lodin aiyukan su da ƙyuiya tare da sanin cewa akwai waɗanda suka maida bayun su ya sanya suka ƙi motsawa suyi aikin ," Da ɗibo ruwa da suka tadda an tada injin yamma kenan suka fara , kafin yakaka ta ɗora da wankin kayan yaran fanne na kashi da fitsari , ita kuma falmata ta tafi aiken da ajus tayi mata wurin saurayin ta wanda shi ma a cikin sansanin nasu dai yake amma yana ta bangaren maza da yake chan-ciki inda tantunan maza yake ," Wannan shine karo na huɗu da ajus take aiken falmata ta karbo mata kuɗi koh kuwa ta tambayo mata saurayin nata kou zasu samu damar haduwa a wannan ranar idan dare yayi ," wanda ita kuma sam falmata bata son zuwa wurin tantunan samarin saboda wani da bata kai ga sanin sa ba da yake biyo ta a baya ta tsakankanin manyan bishiyun darbejiyar yana taɓa mata jiki ," yana faɗin wai tsarin jikin ta tun tana ƙarama yana da kyau ," Sai dai tsoron ajus ya hana falmata tayi wani yunƙuri na samarwa kanta damar kaucewa zuwa aikin , Cikin sanyin jiki ta kama hanya bayan ta biya ta sanarwa yakaka wacce take ta faman gurzar wanki ta gefen ɗakunan su duk da duhun dare da ya riga ya shigo domin har an idar da sallar magariba ina shirye-shiryen yin isha'i amma su koh sallar magaribar ma basu samu damar yi ba kamar yadda a yawancin lokuta haka take faruwa sai dai su haɗa magariba da isha'i suyi tare , abincin dare kuwa ba kullum.suke samun damar ci ba saboda ana idar da magariba ake zubo shi a daka wawaso kamar yadda aka saba , su kuwa a mafi yawancin lokuta basu kammala aiyukan bautar da ake basu ba ,"dan haka zuwa yanzu sai rana ɗaiɗaiku suke cin abincin sansanin kuma basu wani damu sosai ba sakamakon suna da ƴan kuɗaɗen su a kulle ," kou yagana da take take da damar cin abincin ma bata cika shiga cikin turmutsutsun ayi kokawar ɗibar loma da ita ba , a cewar ta daman dole ne ta sa take cin wannan cinkusasshen abincin marar daɗin ɗanɗano ," Tafe take tana juya jikin ta a hankali kamar yadda yake halittar jikin ta , duk da ƙarancin shekarun ta  da yanzu ne ta fara fidda alamun budurci ," amma haka halittar ta take irin matayen da suke da maɗaukakin kyaun diri da ɗan madaidaicin tsawo ," tafiya take cikin nutsuwa baza a taɓa zaton makauniya bace ," saboda yadda take tafe babu ɗan jagora kuma babu sanda sai dai lokaci-zuwa-lokaci ta kan ɗan lalubi hanyar wanda hakan yake babbar baiwar da Allah ya yi mata , tana daga cikin makafin da Allah ya basu ikon gani da zuci , wanda kai tsaye baza'a kira hakan da gani ba domin ba ganin suke ba sai dai wata irin baiwa ce da ɗaukakar ubangiji da ya yi musu daga kwakwalwa zuwa zuciyar su ," Ta tsakanin dattin ganyen bishiyar ta ratso har ta bullo a gaban tantunan da suke duk a rurrufe saboda ɗan sanyi sanyin damina uwa uba tsoron kar muggan ƙwarin damina su buwaye su , " Tsayuwa tayi a dai-dai bakin tantin da take hasashen nasu saurayin ajus ɗin ne tare da yin sallama cikin maɗaukakiyar murya ta kwala kiran sunan sa kamar yadda ta saba ," Daga ciki ya jiyo tare da shaida muryar ta nan take ya fito , nan ta isar masa da sakon ajus ɗin da take tambayar neman sanin kou yau zasu haɗu su zanta ? Inda shi kuma ya faɗawa falmata ta sanar da ita shi yau bai jin daɗi . Tana kammala jin amsar sa ta juya tare da nufar hanyar komawa , signal saurayin ajus yayi wa wani saurayi ɗan uwan sa da yake tsaƴe a gefe wanda kuma tare suka fito daga tantin ," shafa shukurkuɗaɗɗan daddauɗan gemunsa daya saurayin yayi lokaci guda suka yunƙura tare da rufawa falmata wacce ta ɗan fara nisa daga da'irar su ," Ta cikin takun su da yake sauka akan busassun ganyayyakin ta fahimci akwai mutane fiye da ɗaya a bayan ta wanda bata kawo hakan a zuwan wani abu ba cikin ranta ," Cigaba tayi da tafiyar ta , sai dai kome ya tsaya mata ne lokacin da taji anyi sama da ita an ɗaga ta cak lokaci guda ana me sanya hannu a toshe mata bakin ta , kafin taji an  zura da gudu da ita zuwa wani bigire da bata san ina bane duk kuwa da wuntsil-wuntsil da ƙoƙarin sauka da take daga kafaɗun wanda ya ɗaga ta da bata kai ga nasarar saukar ba  ,," sauke ta aka yi akan wani abu da tashin hankalin bai bari ta fahimci menene ba , kafin kuma tayi aune taji an fara ƙoƙarin raba ta da suturar ta alhalin bakin ta yana danne cikin hannunwan wani daban , an hana ta damar ihu , wani irin bugawa zuciyar tayi tamkar zata fashe lokacin da ta fahimci mummunan nufin da suke son aiwatarwa a gare ta ," Bugawar zuciyar ta ya zo dai-dai da na yakaka da tata zuciyar ta fara sauya salon aikinta tun daga barin falmatan gaban ta zuwa yanzu da zuciyar tayi mummunan bugawa, " zuruf ta miƙe tare da zare hannun ta daga ruwan wankin ta kai hannayen nata duk biyu ta dafe kirjin ta ,"......! #Fikrh #umm'muaz #son so [6/24, 10:57 AM] +234 701 013 7848: Fikrah writers association MAFARI ........ ( Hargitsin Rayuwa....) Umm'muaz 15 Dafe da kirjin ta da yake cigaba da bugu ta nufi hanyar da zata sada ta da ɗakunan kwanan mazan sansanin su , domin haka kawai ta ji hankalin ta bai kwanta ba da rashin ganin ɓullowar falmata har yanzu dan haka ta tafi domin ta taro ta su dawo tare,' Sai dai har ta cimma ɗakunan bata ga falmatan ba , sai tsirarun mutane da suke giftawa ta cikin duhuwar ," turus ta jaa ta tsaya saƙe-saƙe ta fara yi a zuci ,"    Toh ina falmata tayi ?    Koh dai ta koma ɗakin su ne wurin ajus ? Ganin bata ga koh alamar ta ba kuma ga shi babu wadatar kafafun mutane a wurin bare ta cigita , ga kuma duhun dare da take tsorace da shi , sai ta juyo gami da kamo hanyar komawa da nufin zuwa ta duba ɗakin su falmata , A sanyaye take taku saboda har yanzu zuciyar ta bata bar tsinkewa ba sai ma ƙara dukan uku uku da take yi ," Bata yi nisa ba ta tsinkayo wani rishi da alamun fitowar kukan da aka ƙi bada dama ya fito ,' kiƙam ta jaa ta tsaya tare da sake kasa kunne lokacin da ta sake jin irin rishin ," a firgice ta juya laɓɓan bakin ta suna furta sunan ,"Falmata" Tayi diri-diri cikin rarraba idanun ta a kewayen wurin ,tana neman inda zata gan ta domin tabbas kunnuwan ta muryar falmata suka jiye mata ," Cikin rashin sanin gaba zata yi ko baya ta taka da gudu tare da hawa kan barandar wasu tsoffin ajizuwan da suke gefe da ita waɗanda kou rufi babu a kan su ta wasu wuraren ma sun fara zaftarewa da alamun sun zama kango ," Da gudu take shiga cikin ajizuwan  tare da kwala kiran sunan falmata , sai dai bata tarar da kome cikin ajizuwan sai tarin bola tare da yanar gizo-gizo da tayi dafifi a ciki , cikin tashin hankali ta jaa ta tsaya daga karshen barandar da take daf da katangar makarantar , daddagewa tayi ta sake ƙwala kiran sunan falmatan , sai dai bata kai ga rufe bakin ta ba taji an ɗauke ta da wani kakkarfan mari , kafin ta farga taji an shatile kafufuwan ta , ta tafi ta baya ta faɗi ƙasa tare da bige ƙeyar ta da katangar  makaranta , zuruf ta miƙe bata koh ji alamun zafi ba lokacin da tashi sautin muryar falmata ya fito tar cikin wani irin kukan wahala tana ambaton sunan ta a kurkusa da ita ," Taku biyu ta ƙara ta ci karo da ita a kwance cikin tarin busassun ganyayyakin da ake sharewa a tara a wurin ya zamto tamkar bolar zuba ganye ," Ɗago ta tayi ta tarairayo ta tare da rungumo ta zuwa cikin jikin ta tana yi tana waige-waigen jin ta inda waɗan da suka bige ta zasu bullo wanda take da tabbacin sune suke shirin cutar mata da falmata cikin ran ta tana jin karfin yin ɗauki ba daɗi da ko su waye domin ta tseratar da falmata ," Tunanin ta ya tsaya chak ! Lokacin da ta ji gaba ɗaya kukan da falmatan take yi ya gauraye da wani irin numfashi tamkar na me shiɗewa , jijjigata ta fara yi tare da kokarin tayar da ita tsaye ,tana cewa        "sannu falmata me suka yi miki ? Duka ? Kin ji ciwo ne falmata tashi muje ki shaa ruwa ," Rinjayar ta falmatan tayi a domin ta gaza tsayuwa sakamakon numfashin ta da yake sarƙewa , su duka biyu suka zube ragwaf a ƙasa kafin falmata tayi baya lau ta tafi zata kwanta cikin sauri yakaka ta riƙo ta kwakwalwar ta na son fahimtar me ke shirin faruwa da ƙanwar ta ? Jijjigata ta fara yi cikin zubar hawayen da suka balle sakamakon tashin hankalin ganin falmatan a kwance bata motsi sai wani irin shiƙar numfashi take ,"   Cicciɓar falmatan take son yi amma ta kasa saboda tayi mata girma da nawi baza ta iya ba , kwantar da ita tayi ta taka da nufin zuwa ta kira mutane su taimaka mata , har ta yi taku biyu a gigice ta sake juyowa , zuciyar ta na bijiro mata da hoton gawar mahaifinta da ta bari a wuri makamancin wannan cikin "gona babu kowa ," Da gudu ta taho gami da sake durƙusawa tare da ɗago falmatan da dukkanin karfin ta , ta rungumo ta a kirjin ta , ta yunkura da kyar ta miƙe gami da ciccibar falmata da jikin ta yake a sake bata motsi , kiki-kiki ta fara kokarin jaan ta ta tafi da ita , sai dai kou taku uku mai kyau bata yi tayi tuntube da wani ɗan kankanin dutse ta baya kafar ta ta zame takalmin ta ya tsinke , suka tafi baki ɗaya suka faɗi ta baya kan falmatan ya bigi haɓar ta nan take hakoranta suka datse laɓɓan ta na ƙasa ya fashe ," Da hanzari ta sake sunkuyowa kan falmata hawayen ta na ɗiga akan fuskar falmatan ta ɗago ta ta fara jaan ta cikin sautin kuka ta fara ƙwalla kiran naiman taimako , domin zuwa yanzu ta fahimci mutanen da suka jefa ƙanwar ta cikin wannan mummunan yanayin da zuciyar ta taki aminta da falmatan ta mutu kamar yadda ta ga alamu , mutanen sun gudu basa wajen ," Da faɗuwa da tashi ta fiddo ta tsakiyar hanyar da ake wucewa , sunkuyowa tayi tare da tallafo kan falmata tana cigaba da girgiza fuskar ta ,"      Meƴe ya same ki falmata ?     Falmata ki tashi dan Allah     Ki tashi falmata ? Ki tashi Hasken tocila ne ya fara hasko su daga nesa kafin mutanen su ƙaraso ," tun kafin tayi magana suka yunƙuro da hanzari suna tambayar ta me ya samu ta kwancen kuma me suke anan ? Cikin kuka take rokon su akan su taimaka su ɗauki ƙanwar ta zuwa asibiti , basu yi ƙasa a guiwa ba suka ɗauki falmatan chak tare da kai ta ɗan ƙaramin ofishin da aka tanada a matsayin ƙaramin asibitin bada taimakon gaggawa ,' Yana zaune yana kammala shigar da wasu muhimman bayanai da suka shafi aikin sa ta computer suka faɗo masa duuu babu sallama bare neman izni ," Da ido ya bisu har suka shimfiɗe ta akan ɗan siririn gadon da aka tanadar domin marasa lafiya ," suka yi tsaye charko-charko sun tasamma mutane ishirin a cikin ofishin a tsai-tsaye banda waɗan da suke daga wajen baranda da idan aka haɗa zasu kai rai hamsi duk ƴan rakiya ne ," Cikin nazari yake kallon su ɗai-ɗaya ta cikin farin gilashin da yake manne akan fuskar sa bayan ya rufe computer gami da tokare hannuwan sa biyu akan teburin ya ɗago haɓar sa da su , cikin ranshi yana jimanta rashin hankali da gidadanci na wasu mutanen ƙauye ,"    Chan daga waje yake jiyo tashin ƴar siririyar muryar ta cikin kuka tana ambaton sunan "Falmata''wanda hakan ya sa da sassarfa ya nufo marar lafiyar da aka kwantar da bai kai ga sanin meye ya faru da ita ba ," Da taimakon hasken ƙwan lantarki fari sol da ya haske ofishin ya shaida fuskar ta duk da cewa ta ɗan kunbura a sakamakon shatin yatsu da suka kwanta tar a gefen da gefen fuskar ta ta da kuma laɓɓan ta da suka ɗan kumbura ,"amma hakan bai hana shi gane ta ba ," Me ya same ta ?? Ita ce tambayar da ya jefo musu a dai-dai lokacin da ya ɗauko abun auna bugun numfashi ya ɗaura shi a saitin kirjin ta ,' kallon-kallo aka shiga yi tsakanin mutanen da suke a cike a ɗakin domin duk cikin su babu wanda ya san takamaimai meye ya faru ga falmatan Ganin sun yi shiru ya sa shi sake cewa " ina ƴan uwan ta ?    Mutane biyun da suka ɗauko ta suka ce ƴar uwar ta tana waje ,"   " Ku ƙira ta" Da kyar ta samu hanya ta kutso cikin ɗakin idanun ta na yararin ruwan hawaye har ya jiƙe gaban hijabin ta , Gaban gadon da falmatan take kai ta zo ta tsaya ba tare da ta lura da wanene likitan ba ita dai babban burin ta ,  ta ga falmata ta motsa tsoron ta tare da taraddadin ta kar ace mata wani mummunan abu ya faru ga ƴar uwar ta , Tun da ta shigo yake bin ƴar siririyar fuskar ta da kallo , daga ƙarƙashin ruhin sa yana zumuɗin kallon cikin ƙwarar idanun ta ," Me ya same ta ? ,"   Itace tambayar da ya jefa mata bayan yaƴi umarnin ga sauran jama'ar akan su basu wuri zai yi aikin sa , maida duban ta tayi gare shi ,"karaf suka haɗa ido ," Tiryan-tiryan ta shiga bashi labari , yayin da shi kuma ya duƙufa wurin bada dukkanin taimakon gaggawar da yake ganin yakamata ga falmata sai dai falmata bata motsa ba ," Zama yayi tare da ɗaukar wayar sa kira yayi tare da bada umarnin tahowa da motar asibiti domin ya fahimci matsalar falmata ta zarce ƴan kayan aikin da suke nan ," kallon sa ya mayar ga fuskar yakaka wacce tayi jazir sakamakon kukan da take ta faman yi ,"     Kiyi hakuri ki daina kuka ƙanwar ki ta samu attack ne na ciwon ta a sakamakon toshe mata hanyar numfashi da aka yi wanda ya jawo huhunta ya wahalta kasantuwar daman tana ɗauke da cutar asthma amma insha Allah zata samu sauki numfashin ta zai dai-daita yanzu motar asibiti zata zo akai ta babban asibiti domin bata cikakkiyar kulawar da ta dace da masu irin ciwon ta sannan kuma jami'an kiwon lafiya mata su duba ta domin cikin bayanin ki ina zargin ta faɗa hannun ƴan ɓata gari ne," Tun da ya fara bayani yakaka take ƙara sautin kukan ta zuwa lokacin da ya gama mata bayani kuwa sosai take kuka har tana shiɗewa sakamakon ji da tayi falmata tana ɗauke da wata cutar da har sai an dangana ga babban asibiti ,'kuka take bilhakk . Komawa yayi ya zauna tare da jingina da jikin kujerar sa bayan ya rintse ƙwarar idanun sa , saboda sosai kukan ta yake taɓa masa ruhi , gashi kuma bai san yaya zai yi da ita tayi shiru ba , Cikin abunda yake ƙasa da mintuna sha biyar motar asibitin ta iso aka shigar da falmata cikin motar tare da yakaka wacce taƙi fur ta saki jikin falmatan da zuwa yanzu numfashin ta ya fara komowa amma sama-sama , Suna zuwa babban asibitin gwamnatin jaha ,aka ƙarbe ta tare da shigar da ita ɗakin bada taimakon gaggawa karkashin ƙulawar dakta hamza da daman ya kasance babban likita ne shi a asibitin , zama dirshan yakaka tayi akan tiles ɗin wurin tare da dunƙulewa wuri guda ,bata ko damu da mutanen da ta zo ta tadda a wurin da su ma suka kawo marasa lafiyan su da kuma sauran mutane masu wucewa da suke mata kallon tausayawa ba , Bayan share zaman mintoci arba'in da ƴan kai , wanda yakaka baza ta iya fasalta iyakacin ruɗani da hargitsin rayuwar da ta shiga ba a ƴan mintocin , dakta hamza ya fito cikin alhini da rashin kuzarin da fargaba suka haddasa mata ta ɗago idanun ta da suka kumbura tana tuhumar sa da su domin ta gaza buɗe baki ma tayi magana ," Ɗan lallausan murmushi yayi tare da yafitar ta da hannu ," a sanyaye ta miƙe tana gama hanya ta bi bayan sa zuwa cikin ainahin ɗakin ," Daga bakin kofar ta jaa ta tsaya lokacin da ta hango falmatan ras a zaune a bakin gadon asibitin,wata irin dariyar murna ce ta subce mata kafin ta taka da gudu ta tsalleƙe ƴar tazarar da take tsakanin su tare da rungumo falmatan wacce ita ma ta washe ƴan haƙoran tana dariya da jin sautin dariyar yakakan da take nema tun da ta farfaɗo , fuskar ta sayau da alamun rashin kuzari a tare da ita sakamakon allurorin da ta shaa har da ƙarin ruwa ," Falmata nah sannu , sannu sannu dan Allah me suka miki ?? Wacce irin cuta ce take damun ki falmata ciwon ki ya tsorata ni , irin tsoron da zan iya mutuwa idan ya zarta haka dan Allah falmata kar ki sake irin wannan rashin lafiyar ," gaya min ina ne yake yi miki ciwo yanzu , meye suka miki ?? Dakta hamza wanda yake tsaye ya harɗe hannunwan sa a kirji yana kallon su , karon farko da yaga wata irin tsaftatatciyar zallar ƙauna a tsakanin ƴan uwan biyu ,"shi ya amsa mata dukkan tambayoyin ta . Cutar asthma ce take damun ta , asthma cuta ce da take kama huhun mutum ya zamana huhun mutum yana kumburi tsokar huhun tana matsewa tare da rurrufe hanyoyin da iska take shiga wanda hakan yake bada matsala wurin shiga da fitar iska / numfashin ɗan adam , alamomin cutar sun haɗa da tsananin tari musamman cikin dare zuwa wayewar gari , gwarnaki , da kuma ɗaukewar numfashi ko kuma yin ƙarancin sa , ana iya gadon cutar asthma ta iyaye , ana kuma iya samun cutar ta hanyar ƙura idan tayi yawa , ko ta hanyar shaƙar iskar gas , ko kuma tsananin sanyi , cutar asthma bata da wani maganin warkar da ita baki ɗaya sai dai akwai magungunan hana samun farmaƙi daga cutar ," sannan ya zama dole me cutar ya kiyaye kan sa daga shaƙar ƙura ,shaƙar iskar gas ,zama cikin wurin da yake da tsananin sanyi ko kuwa shan abu mai matsanancin sanyi domin bawa kansa kariya daga samun farmaƙin ciwon ," Numfasawa yayi yana me gauraye idanun sa cikin na yakaka wacce tayi kasaƙe tana sauraran sa idanun ta tar akan fuskar sa , lumshe idanun sa ya sake yi lokacin da ya ji wani yanayin shauƙi yana fusgar sa a sakamakon kallon cikin idanun ta da hasken ƙaton farin ƙwan wutar da yake cikin ɗakin ya haska su suke wani irin sheƙi tamkar ba yanzu suka gama ambaliyar hawaye ruwan ba ," Sannan ƴan bata gari sun yi yunƙurin lalata ƴar uwar ki ta hanyar yi mata fyaɗe sai dai a binciken da muka gudanar basu riga sun cimma nasara ba ,Allah ya kiyaye ta sai ku kula da gaba ,  ga sister zahra zata sake yi muku bayani dalla-dalla , zaku kwana anan zuwa gobe da safe muga yanayin jikin nata sai mu sallame ku , Duk da cewa ba duka kalmomin sa yakaka da falmata suka gane ba amma sun fahimci dai falmata tana da wani ciwo wanda yake riƙe numfashi a irin fahimtar su , sai dai daga yakaka har falmata babu wacce ta wani damu sosai saboda suna ganin ta samu sauki saboda falmatan ta bada tabbacin bata jin kome a halin yanzu lafiyar ta ƙalau sai ko ɗan rashin karfin jiki dan haka su ran su yau ƙwal zasu yi kwanan sabon wuri kwanan ƴanci , kwanan cikin haske , ga falmata kwanan kan gado da katifa duk da ba wani taushi bane da katifar asibitin amma ga falmata abun daɗi ne tun da kuwa yau ne karon farko da ta hau gado da katifa a gaba ɗaya tarihin rayuwar ta ,"dan haka da walwala akan fuskokin su suke yiwa dakta hamza godiya wanda yake bin su kawai da ido tare da gƴaɗa kan sa ,"ya kuma juya yana mai sake jaddadawa wata ma'aikaciyar jinya wacce ya kira da suna zahra akan ta tabbatar tayi musu bayanin kalmar fyaɗe tare da nisantar hulɗa da duk wani ɗa namijin da ba muharramin su ba , "wanda shi da kan sa bai san dalilin da ya sa yaji ya damu akan son su nisanci hulɗa da maza har yake jin da yana da dama da ya killace yaran , sai dai kawai ya ɗauki hakan a zuwan tausaya musu da ya fara yi da fahimtar da yayi basu da wani gata bayan Allah sai su biyun da junan su suka dogara ,' Har ya taka ya nufi bakin kofar ficewa daga ɗakin bayan yayi musu sallama domin barin asibitin , sai kuma ya juyo gami da nufo wurin da yakaka take zaune akan kujera daga gaban gadon falmatan ," Janyo wata kujerar yayi tare da zama a daf da yakaka wacce tayi wuri wuri tana tunanin me kuma zai sake zaunar da shi ? Domin ita dai sam bata sakewa idan yana wurin wani irin nawi take ji daga ƙarƙashin ran ta da zuwa yanzu ta kasa fahimtar menene , abu ɗaya ta sani shine daga farkon haɗuwar su da tsiya suka faro ta tare da kullatar shi gami da jin tsanar sa cikin ruhin ta, sai dai daga ranar da ya fara taimakon ta zuwa yau ,ta kasa sanin takamaimai a wane mizani ta ajiye shi , ta dai san ƙwarai ta fara ganin girman sa daga haka baza ta ɗorar da kome ba bayan faɗuwar gaban da take ji a duk lokacin da idanun su suka sarƙe cikin na juna , shi yasa sam bata son kallon idon sa , Umarni ya bada aka miƙo masa ƴan kananun kayayyakin wankin ciwo idanun sa akan laɓɓan ta da na ƙasan ya kumbura ," Da kansa ya wanke mata ciwon da ta ji a sanadin dartse laɓɓan , yana yi yana kallon idanun ta da suke runtse gam a saboda ɗan radaɗin maganin wanke ciwo , a hankali kalmar , "sannu" ta subto daga bakin sa bayan da ya gama wanke mata ciwon ,yana bin fuskar ta da kallo ," ya daina zafi ko ? A hankali tana me kaucewa kallon idanun sa ta 'gyaɗa kan ta ," nagode Miƙewa yayi ,"ki zo ki sayo muku wani abinda zaku ɗan ci a waje ," Tare suka jero duk inda suka wuce tsirarun ma'aikatan asibitin da suke aikin dare , sai sun isar da gaisuwar su , har suka fito bakin asibitin babu me cewa ƙala a tsakanin su ," zaro gudan dubu ɗaya yayi a aljihun sa ya miƙa mata tare da gwada mata tsallaken titi wurin wasu mata masu toye-toye da kuma masu sayar da shayi ,     Tare da ɗan durkusawa ta miƙa hannu biyu ta karbi kuɗin tana godiya , bin bayan ta yayi da kallo har sai da ta tsallaka titin kafin ya juya cikin asibitin inda ya ajiye motar sa ya shiga gami da bata wuta ya bar harabar asibitin ,' Bayan sun ci masa/waina tare da ruwan bunu shayin da yakaka ta sayo musu a waje , sai suka tattara hankulan su baki ɗaya ga sister zahra da take yi musu bayani dallah-dallah game da fyaɗe ta kuma tsoratar da su sosai game da yin tarayya koh wasannin banza da maza , sun kuwa tsoratu har cikin rayukan su fiye da zaton ta domin su dukkanin su biyu kwana suka yi tare da tunanin maganganun da ta faɗa musu , wanda ya sa suka ji baki ɗaya zaman sansanin nasu ya fita akan su , ga zaton falmata mazan sansanin su ne kaɗai suke iya yiwa mace fyaɗe su yi mata ciki ,"     Yakaka nikam bazan koma sansanin mu ba dan Allah mu samu wani waje mu dunga kwana koh aina ne ' cewar falmata kenan lokacin da gari ya waye likitocin aikin safe suka zo suka duba su tare da basu sallama bayan sun tabbatar da ta samu lafiya ,bata kuma cikin hatsari ," Nisawa yakaka tayi wacce itama har ga Allah bata son komawar sun sansanin su , ko kusa bata son abun da zai ɓata rayuwar falmata , duk wani abun da ya shafi falmata bata ɗaukar sa da wasa ," Falmata nima bana so mu koma sansanin mu , toh amma bamu da wurin zuwa da ya fi chan ɗin , bamu da kowa ba mu san kowa ba ," Mu tafi wurin uwarɗakin ku yakaka , mu roƙe ta  , ta yadda ta bamu wurin kwana koh da a zaure ne , Zubawa falmata ido tayi tana juya shawarar ta ta cikin nazari , tana hasashen madam saly baza ta ƙi taimakon su ba toh amma gidan madam saly ma ai sansanin maza ne , mazan ma tambaɗaɗɗu ƴan iska , har ma gwara na sansanin su ," Girgiza hannun ta falmata tayi , ta ɗago ta dubi fuskar falmatan da hawaye ya silmiyo ,"   Yakaka dan Allah kar mu koma sansani , ajus baza ta daina aikena wurin ƴan maza ba ni kuma tsoro nake ji yakaka dan Allah kar mu koma ," Da sauri ta sanya hannu ta goge mata hawayen ,"kiyi shiru falmata baza mu koma ba ," A hankali suka tako zuwa wajen asibitin , duk da cewa yakaka ta so su jira dawowar dakta hamza domin ta bashi chanjin sa naira ɗari takwas da yake hannun ta , toh amma kukan falmata ya kaɗa mata hankali bata jure damuwar falmata , sai dai har zuwa yanzu da suka fito bakin titin suka jaa suka tsaya hankalin ta ya kasa kwanciya da zama a gidan madam saly tare da ƙanwar ta , Kamo hannun falmatan tayi ta zaunar da ita lokacin da wani tunani ya ɗarsu a ran ta ,"    Zamu je gidan madam saly mu roƙe ta mu zauna zuwa wani ɗan lokaci , sai dai da sharaɗi falmata , Sharaɗi ?   Eh sharaɗi falmata , gidan madam saly matattarar ƴan maza ne , ba kamar yadda kike zato bane falmata , gidan madam saly gidan ƴan iska ne , kin ga ke kuma falmata baki da lafiyar idanu zasu iya cutar da ke kamar yadda na sansanin mu suka so yi , dan haka na samo mana wata dabara , idan zaki yadda , Zan yadda koma menene yakaka idan har baza mu koma sansanin mu ba ," Zaki koma namiji falmata Zaki koma saka kayan maza Zan aske miki kan ki , domin ta haka ne kaɗai a yanzu zan iya kare ki daga ƴan maza kin yadda ?? Baki buɗe falmata ta ware manyan idanun ta tana juya su a saitin wurin da take jiyo sautin muryar yakaka tamkar dai tana kallon ta ,' !!!! .    Kar ku manta da kankaro mutunci , Iya adadin sharhi da nuna kulawar ku iya karfin da zan samu wurin cigaba da rubutu      Nagode. #umm'muaz #fikhr #son so[6/24, 10:57 AM] +234 701 013 7848: Fikrah writers association MAFARI... ( Hargitsin Rayuwa) umm'muaz 16 Tafe suke su biyu akan hanyar su ta zuwa gidan madam saly , idan ba wanda yayi musu farin sani tar-tar ba , babu ta yadda za'a yi a gane falmata mace ce , sakamakon askin tal kwabo da yakaka tayi mata da sabuwar rezar da ta saya , sai walwali da ƙƴalli mummulallen kan ta yake , jikin ta kuwa sanye take da wasu afarangiya da wondo na maza da suka yi mata bururum-bururum wanda yakaka ta saya mata a kasuwar tsaye da sauran chanjin dakta hamza , Fuskar falmata sam babu walwala saboda dole kawai yakaka tayi mata har ta amince kan ta ya sha askin da tun da aka yi mata shi take jin kan ta sakayau tamkar zai faɗo ga uwar ranar damina da ta fara ɗagawa "hantsi ya dubi ludayi" , wannan karon hantsin kan falmata ya duba ," Yakaka nikam gaskiya bazan iya sake yadda ki min wani askin ba idan har gashi na ya sake fitowa kamar yadda kika ce ,"saboda gaskiya zafin rana tana ƙona min fatar kai ,sannan kin ga kullum a rana nake wuni a zaune ," Cikin tausayawa tare da ganin laifin kan ta yakaka tace ,"    Ki daure kiyi hakuri falmata ni da kaina ba'a son raina ba ne na aske miki suma ,bamu da wani zaɓi ne bayan hakan ,kina sane dai da yadda mazan gari nan suke ƴan iska ," kiyi hakuri nan gaba bazan sake suɗe miki kai tal kamar haka ba zan dunga bar miki kaɗan ,"     Me zai hana ki saya min hula kawai ?? Ki barmin kaina ba tare da kin aske ba idan ya so na cigaba da sanya kayan mazan a zuwan ni tamiji ce , tunda ba wanda ya san mu a gidan madam ɗin sai yagana da kolo ," Yakaka bata samu zarafin amsa mata ba sobada sun kawo gidan madam saly ,       Cikin yin ƙasa-ƙasa da murya tace kiyi shiru falmata mun zo gidan , kar kiyi wani abun da zai sa wani ya fahimci ke mace ce ,"   Fuska a turɓune falmata tace " toh" Tun kafin su ƙaraso ainahin cikin gidan suka soma tsinkayo muryar madam saly wacce take ta bala'i da dure-duren ashariya akan satar da ta wayi gari an ɗunguma mata har ta naira duba ishirin ," Ƙarasowar su ta zo dai-dai da cewar madam saly ," kuma na rantse daga yau duk wasu ƴan zaman fara ƴan zaman alfarma su nemi inda dare yayi musu tun da abun ma ya zama haka , kayi wa mutum rana yayi maka sulusin dare , ji min ganin arhar gabas ? daga yau babu shegiyar ƙaramar karuwa da zata sake kwanan min cikin gida kun dai ji na rantse ai daman kome aka yi da sabara sai ta yi kere," ta karasa tana sake shigar da mici-micin idanun ta da suka yi jaa domin bala'i ! Duk da yakaka ba duk kalaman madam saly ta kai ga fahimta ba , amma ganin ta cikin maɗaukakin bacin rai ya haka , yayi matuƙar tsorata ta tare da dukushe mata ƴar ƙwarin guiwar tunkarar ta da batun dawowar su zama a wurin ta ," A fusace ta juya ga su yakaka lokacin da taji yakakan tana gaida ta bayan ta ɗurkusa guiwar ta biyu a ƙasa ,"        Ba tare da ta amsa mata ba ta maida ganin ta kan falmata wacce take tsaye kiƙam tana jujjuya idanun ta kan nan sai sheƙi yake tare da ɗaukar idanu.,' Wannan ɗan ƙolon fa ? Shi kuma daga ina ?? Cikin sanyin murya da inda-inda yakaka tace"  ƙani na ne " tana mai sanya hannu ta jawo hannu falmata ta ɗurkusar da ita ,"      Ina kwa..... Ko kafin falmata  ta ƙarasa kalmar gaisuwar da ta ɗauko nufin yiwa madam saly , tsawar ta ta katse mata hanzari ,"     Miƙe miƙe maza-maza ka kama gaban ka , ka tafi barar ka ni nan bani da buƙatar irin ku , ke yaks ɗan uwar ki wane ɗan iskan ne yace ki kawo min ƙanin ki nan ? Ko nace miki ina bukatar almajiri ne ? Oya kama hanyar ka kayi tafiyar ka kwa haɗu a mahaɗar ku kar na sake ganin ka a gidan nan ," Gaba ɗayan su sun firgita da tsawar da tayi musu musamman ma falmata wacce kalma korar da aka yi mata ta sanya ta jin ruwan hawaye ya fara taruwa a gurbin idanun ta ," Madam kiyi hakuri , shima na kawo shi ne ko akwai aikin da zai dunga yi miki ,?         Aikin ubanki wannan ɗan tatsitsin yaron zai min ? ,"     Kai tashi kayi naka guri nace ," ta furta hakan tana zazzarowa falmata ido ,wacce dirin muryar madam saly cikin faɗa duk ya bi ya diririta ta tare da dasa tsoron ta cikin ran ta anan take har ma ta ji ta fara nadamar zaɓar gidan ta a matsayin wurin mafakar ta , Cikin muryar kukan da ya bayyana kansa yakaka tace ,"      Makaho ne madam dan Allah ki taimaka mana ki bamu wurin da zamu dunga kwana wallahi zan dunga yi miki aiki daga safe har dare koh baki biyani ba ni dai kawai ki taimake mu ni da ƙani na ki bamu wurin kwana ,? Kallon hadarin kaji madam saly take yi ma ta ,"     Yau ji min gantalallun yara ke yanzu ni ce zan baku masauki ke da musaƙin ƙanin ki ?? Dan uban ki yaks kin ga gida na yayi kama da masaukin baƙin ƴan gudun hijira ?? Ciki ma har da muskinai ? Ke ma ai kin sa wanan abun bazai yi yu bane "auren mage da ɓera " an faɗa miki nan gidan sarkin unguwa ne koh kuwa gidan mai gari ?? To bari kiji ni bani da wurin ajiye ke kan ki bare miskinin ƙanin ki , toh na ci uwar me da ku ??gayyar na ayya gayyar tsiya gayyar ƙwarƙwata da tsumma, dan aikin da kike min daga na ɗaga murya nayi cigiya zan samu madadin ki , dan haka tun wuri ki maida ƙanin ki inda kika ɗauko sa ,ki zo ki kama min aiki na , kina cin lokacin aiki kin kuma san dai doka ta ban yadda da asara ba ," Ɗan liti wanda tun shigowar su yake tsaye a gefe ya kafe yakaka da falmatan da idanu ,yana nazarin ɗan dirarren yaron mai ƴar kyakkyawar zagayayyar fuska da yakaka ta kira da kanin ta ," yayi charaf ya chafe zancen jin ana shirin korar masa hanyar samun abebaɗan arziki ! Haba haba madam saly tayaya arziki yana bin ki kina guje masa ," kuma ai a so kare har bindin sa !      Ya furta hakan yana farfari da ido A harzuƙe madam saly wacce ta koma daga bakin kofar ɗakin da ƴan matan ciki ke tattataro ƴan kayayyakin su suna fitowa ta juyo ,' waɗan nan ne hanyar arzikin liti bana son ƙazamar kalma," wai me kuke jira ne ?? Ta wurga tambayar ga yakaka wacce zuwa lokacin kuka take yif-yif suna durkushe cikin rana ,"   Ke dai mutuniyar mu sanya labule ki ji bayani , kiji nufi na kar ki yanken hukunci baki ji hujja ta ba ,!"idan ban da abun ki ai Abun da ke ga amarya shi ta kan ba ango "  Ya furta hakan yana jan hannu madam saly wacce take wurga masa harara ,tamkar idanuwan ta zasu faɗo ,"   Bayan shuɗewar mintoci sha biyar madam saly da ɗan liti suka dawo ,"     Ke yaks na yadda ki zauna anan tare da su larki a ɗakin su , zasu ɗan matsa miki wajen kwana domin wannan babban ɗakin kulle sa zan yi , ƙanin naki kuma zai bi ɗan liti su dunga kwana tare idan ya so kullum da safe ya dunga zuwa nan yana min wanke-wanke kafin ya tafi barar sa ," daga yanzu bazan biya ki ko sisi ba domin zan dunga ciyar da ku sau uku a rana da ke da ƙanin naki ,idan kin yadda toh idan kuwa baki yadda ba sai a bi wani sarkin ,! Ba tare da tunanin kome ba yakaka da falmata suka amince bayan sun bi ɗan liti da madam saly da doguwar godiya tare da addu'o'i , Toh sai ƙanin naki ya biyo ni yaga ɗakin kwanan koh ? duk da dai ba gani yake yi ba amma ya ɗan tattara wajen da zai sa ƴan haƙarƙarin sa ," ni ya ma sunan sa ne ??    sunan sa kachalla !     Ah kachallari ne toh tashi zo mu tafi mikon hannun ka ," Tare da rashin sakewa falmata ta jefa hannun ta cikin na ɗan liti , wanda ɗumi tare da laushin fatar hannun falmata tuɓus-tuɓus , suka nemi ruɗar da shi a karon farko ," Da ido yakaka ta raka su cikin ranta tana fatan Allah ya sa madam saly ta zamto gatan su ,! Kichibus yagana suka yi ita da su falmata wacce ɗan liti ya matse mata hannu gam cikin nasa yana ɗan luguiguitawa , a ɗan fisge ta dube su tare da gaishe da ɗan liti sai dai kuma fuskar falmata da ta gani a fisge ya sanya ta sake waiwayowa da zabari sai dai bata ci nasarar sake kallon fuskar yaron ba sai bayan sa ', Tana shigowa ta ci karo da yakaka cikin mamakin ganin ta a wurin aikin tare da alhinin abun da ya faru da su a daren jiya wanda duk a zaton ta har yanzu su yakaka suna asibitin ne ta kamo hannun yakaka ,     Yakaka ya jikin falmata ??tana ina ? Ta samu sauki da fatan babu abun da ya same ta ?? Sai da yakaka ta ɗan hah-hanga ta ga babu kowa a cikin rumfar da suke saida burkutu wanda a halin yanzu take kan tattarawa tare da goge gujeru da teburan da masu saye ke zama ," tace      Yagana jikin falmata da sauki , kuma a halin yanzu tana gidan nan mun taho tare , yagana dan Allah ki rufa mana asiri domin a saboda abun da ya so faruwa ga falnata jiya mun bar sansanin mu mun dawo nan gidan da zama sai dai a matsayin falmata namiji , zaki ganta cikin shigar maza da askakken kai tana amsa sunan kachalla , domin Allah kar ki faɗawa kowa ita mace ce kin ji ? Ki rufa mana asiri !       Tare da maɗaukakin mamaki yagana take kallon ta ,   falmata ta koma namiji kuma ??kuma kun dawo nan gidan da zama ? Anya yakaka wannan hanyar mai billewa da kyau ce ? Kin san fa gidan nan cike yake da ƴan iska da ma unguwar baki ɗaya , ke da kan ki hatsari ne kwanan ki cikin gidan nan kina dai ganin yadda da ƙyar muke kwatar kan mu a hannun ƴan iskan nan idan suka sha kunun madam saly , ni a ganina gwara mazan sansanin mu basa shan wannan ruwan da ke fitar da mutum a hankali ya sa hauka, ni dai idan har kin ɗauki shawara ta ku koma sansani duk lalacewar sa yafi nan , Yagana falmata tace baza ta koma ba , ta riga ta tsorata , sanin halin mazan gidan nan ya sa na ɗauki matakin mayar da falmata namiji domin kare ta daga idanun su ,"     Katse ta yagana tayi ,"    Toh idan kin kare falmata ke kuma fa ?? Bakya tsoron su cutar da ke ??     Ɗan murmushi yakaka tayi ,"    Zan iya sadaukar da kome nawa domin na bada kariya ga falmata , falmata miskiniya ce bata da kowa daga Allah sai ni ,"  ki mana addu'a kawai yagana kuma ki rufa mana asiri ,'      Kallon ta yagana tayi na ƴan dakikai , shikenan dan ta ni kam baku da matsala koh cewa kika yi kar na nuna na san falmata  bazan nuna ba ,  me ma kika ce sabon sunan ta ??     Kachallah     Kachallah , ta maimaita Suka haɗa ido gami da kwashewa da dariya , ga alama zuciyar yakaka ta samu ƴar nutsuwa a karon farko tun bayan barowar su garin su .           Niamey Niger Yau kwanakin su siyama da gnala goma sha huɗu wanda kuma a gobe ne suke da niyyar komawa maraɗi saboda hutun da ta ɗauka a wurin aikin ta gobe yake ƙarewa , Zaune suke a ɗakin ubboh wacce ta kama kan siyamar tana kitsewa kamar yadda ta saba yi mata tun siyamar tana ƙanƙanuwa ,har ɗan tasawar ta kafin a aurar da ubboh ,"       Ho addah ke kouwa yaushe ne zaki bar mini kitson hittoɓe ? Haba mana adda baki ganin na girma da wannan kitson ??      Ɗan murmushi ubboh tayi tana me kallon fuskar siyama da ta shagwaɓe fuskar ta ta jikin mudubi ,"       Kauna ta kin kouwa san yadda kitson hittoɓe yake fidda kyauwou tare da cikar surar ki ?? Na kou jima ina faɗi miki babu kitson da ke haska ki yaa shi ina mai tabbatar miki akwai wani sirri cikin kitson ga ki riƙe shi da kyawou har gidan amren ki," Shiru siyama tayi domin ubboh ta fama mata ciwon da ke nuƙurƙusar ta cikin rayi ," da nazarin sauyin da ya bayyana akan fuskar ta ubboh ta tsaida kitson da ta fara yi ,"      Ban san yauhe ne munka fara ƴar haka da ke ba kaunata ,?? Yauhe ne kin ka fara boye mini damuwar da ke a zuciyar ki ? Yanzu duniya da gaskiya siyama kina da ƴar uwa da ta fice ni ?? Tuno da kusancin da ya wanzu tsakanin mu tun tsawon lokacci shin kou kuowa dai matsayi na ya sauyu gare ki ?   Juyowa siyama tayi ta fuskanci ubboh , fuskar ta da alamun rashin jin daɗin maganganun ubboh ," Kou kussa adda matsayin ki gareni wallah basshi sauyuowa , ke kou me zai sanya ki wagga irin tounani adda amm ??    Shafar fuskar ta ubbo tayi ," cikin ranta ƙaunar siyama na sake linkuwa, Tun zouwar ki nan wurina na fahimci kina tare da damuwa amma juyin duniya nayi da ke ki faɗi min me ke ad damun ki kin ki faɗi mini toh ƙaƙa kike so in yi da rayi na ? Shin kou kuwa dai a chan gida an ka bata miki rayi ??      Ajiyar zuciya siyama tayi domin ta ga wannan ce damar da zata yi amfani da ita wurin fidda abun da ke boye cikin ran ta , sake marairaice fuska tare da shagwaɓe ta tayi bayan ta karya wuya ,"     Adda amm ni kam ban san dalili guda wadda ya sa hamma youssouf ya ƙi jini na ba , tun tasowa ta nake hangen ƙiyayyar da ke mini cikin idanouwan sa       Da sauri ubboh ta kai hannu ta ɗan make bakin siyamar , tare da maɗaukakin bacin rai akan fuskar ta tace ,"     Wanne irin kalami kike haka ga ɗan ouwan ki siyama ? Shi youssouf ɗin ne basshi ƙamnar ki ? Ƙaƙa kin kai ga fahimtar hakan ,?  Ƙou kouwa shi da baki nay ya furta hakan gare ki ? yi samri ki sanar da ni ƙaƙa anka yi wagga mummunan tounani ya kai ga ɗarsuwa cikin rayin ki ?   Hawayen da daman suna kurkusa sune suka samu dalilin ballowa da gudu akan kumatun siyama ," cikin ranta tana faɗin "ayi a ƙare yafi a bari sai gobe ,"     Hamma youssouf bai ɗaouke ni matsayin kauna gare shi ba , har ya gaza boye hakan a gare shi Shi ɗai , sai da ta kai ya bayyana ga bayun masarauta agades , inda ya danganta ni da baƙuwa garai a gaba gare su ,"sun ka maishe ni marar muhimmanci ga har ta kai bayun sun nemi taka ni ,'    Cikin takaicin jin abun da youssouf ɗin ya aikata ga ƴar lelen ta ubboh tace ,"      Yi shirun ki kaunata ki kuma daina wagga mummuna tounani , youssouf yana dawouwa ya iske ni nan cikin gida na zan kuma yi masa magana , yo a rabe magirbin yakuwa ne da na rama ?? Bar ni da shi ,"     Cikin sanyin murya da cikin ran ta ba haka ta so ba , tace     Adda kar ki masa faɗa bissa dilili na bani son ko ƙaƙa ran sa ya baci a sanadiyya ta , bacin ran sa ba zaya dadaɗa mini ba ,"       Cikin son fahimtar abun da ta hango tattare da siyamar ,"ubboh" tace      Ke ko ƙauna ta faɗi min gaskiya ƙou kouwa dai son hamman naki kike ?? Kou amren dangin kike so ?     sunkui da kan ta tayi a lokaci guda tana wani ɗan kyakkyawan murmushin da tun zowar ta ubboh take son ganin irin sa a fuskar ta , kamo haɓar ta tayi ta ɗago fuskar ta ,tana dariya tace      "ni ƴar uwa nake gare ki bai kyautu ba ki boye min kome idan Allah ya yarda youssouf sai ya zama miji gare ki , ina bayan ameren ku ɗari cikin ɗari , ai ba domin lamurran sa da wagga ɗiyar buzouwa ya kankama ba ai da ba'a bawa dawa ba gida ba ta ƙoshi ba ," ki kauda wagga mummunan tounani naki , youssouf ɗan ouwan ki ne kuma zai zamto miji gare ki bisa yarda Allah , ki samu kusanci da shi , kin ji kou ? Ni zan yi maganar ku da hajiya umma ,"      Cikin matsanancin farin cikin da siyama ta gaza boye shi ta miƙe bisa kan guiwar ta tare da rungume ubboh wacce ke zaune bisa bakin gadon ta na alfarma ," zuciyar ta cike da farin cikin da ta daɗe rabon ta da jin irin sa tamkar dai ubboh ta riga ta ɗaura mata aure ne da biyamuradi youssouf ɗin ,"          Nagode nagode nagode , kawai ita ce kalmar da take fitowa bakin ta saboda ta gaza doguwar magana Cikin sanɗa saɗaf-saɗaf gnala ta koma da baya wacce ta taho domin kawo wa siyama lamurjen da ta sanya ta haɗa mata , ta zo bakin kofar ta tsinkayi tattaunawar su da ta jaa hankalin ta har ta tsaya daga bakin kofar ta ji kome ,"      Sai dai kan ta ya ƙulle ashe daman siyama ba ƙanwa take ba ga biyamuradi youssouf ??ashe kishiya take ga uwargijiyar ta ? To amma ya aka yi gimbiya maimouna bata kai ga sanin hakan ba ??    Jikin ta har rawa yake lokacin da ta mayar da lamurjen ɗakin girki tare da komawa cikin ɗakin da aka yi mata masauki ta murza ɗan makulli , cikin ujila ta fiddo wayar ta tare da danna kiran uwargijiyar ta tana me zumuɗin sanar da ita wannan labarin , domin tun zuwan su sau uku gimbiya maimouna na kiran ta a waya tana tambayar ta ko akwai wani labari koh sun koma maraɗi ??ita kuma Tana shaida mata har yanzu suna niamey ɗin kuma bata ci karo da wani abun da ke bukatar fashin ɓaki ba ,"sai tsantsar ƙaunar da ta fahimci tana tsakanin ƴa da ƙanwar, wanda gimbiya maimouna ta gwatsale ta tare da cewa bata tambaye ta wannan ba ta kuma sake gargaɗin ta tare da jaan kunne akan ta kula da abun da ya kai ta kaɗai ,! Sai dai har wayar ta gama karaɗin ta daga chan wurin gimbiyar bata ɗaga ba , "tana kuma jin tsoron sake kiran ta kar tayi laifi , dan haka ta maida wayar tare da dasa zaman jiran kira daga gimbiyar ,!         Maraɗi Lokaci yayi  kusa da zaki iddasa aykin da kin ka faro shi saratu , koh kin manta cikin watan ga mai kamawa youssouf yake cika shekarun sa talatin cif ne ? Kou kouwa dai kin manta da abun da zai faru a ranar zagayowar haihuwar sa na cikon shekarun sa talatin ,     Ban manta ba hajiya uwa ba kuma zan manta ba tou ƙaƙa ma za'a yi na mance wannan lokaci ?bayan shi zai zamto shiri na na karshe akan tarwatsa rayuwar safiyyah tare da duk wasu masu ƙaunar ta ?? Ke dai Allah shi kai mu karfe 23:59h na ranar goma ga wattan biyu ," Ni ma nace Allah ya bani ikon ɗorawa !      Kar ku manta da nunan ƙauna ! #umm'muaz #comment #vote #share [6/24, 10:58 AM] +234 701 013 7848: *©Fikrah Writers Association* *MAFARI* (hargitsin rayuwa) *Umm"muaz* *17* Cikin sati biyu da tarewar su yakaka a gidan madam saly ,sun zama ƴan gari a da'irar ta yadda yakaka ta san ɗakunan manyan kilakai da ƙananun karuwan da suke unguwar saboda aiken ta da madam saly take wurin su , a gefe ɗaya kuma ta zama ƴar ɗakin samy baby , wacce bayan dawowar yakaka gidan madam saly ta gama nazarin yarinyar tsaf , ta gane bata san ma mai kalmar bariki take nufi ba kamar yadda da tayi zaton yakakar ƙaramar karuwa ce , sai ta fahimci ashe yakakan neman abun sawa a bakin salati take tare da wajen da zata sanya haƙarƙarin ta , dan haka sai ta jaa ta a jiki ta maida ta mai gyara mata ɗaki tare da yi mata ƴan kananun aike da aiki , ita kuma tana bata ƴan kuɗaɗe bayan jibgin suturun ta da ta fitar ta bata kwance , tun yakakan tana ɗari-ɗari ganin abun da samy baby tayi mata a farkon haɗuwar su , har dai ta zo ta saki jiki da ita , sosai take kyautatawa samy baby da ta riƙa a matsayin uwarɗakin ta , wacce take samun alheri tare da sakewa a wurin ta , domin a lokuta da dama har ƴar hira samy baby take zama su yi da yaks , Aikin gidan madam saly kuwa tuƙuru yakaka take yin sa domin gwanintar da take nunawa ya faranta ran madam saly da take ganin ta a matsayin ginshiƙin su cikin duniya a yanzu , bata da wani lokaci nata na kan ta sai na aikin burkutu wanda ba'a sanya ba ma yi take kamar su wanke dawa , juya ruwan dahuwar burkutun da kuma tace shi wanke kayan madam saly da gyara mata ɗaki , tun safe idan ta kama aiki sai dare karfe sha ɗaya take samun hutu ," wanda hakan ke matuƙar farantawa madam saly rai har take ganin wautar kan ta da farko,  da ta so korar su ashe dai maganar ɗan liti dutse , Ga falmata ma sai sam barka domin kuwa har ɗan kumatu tayi ta sake mul-mul , sakamakon cika mata ƙundu da ɗan liti yake da cimar daɗi kullum dare kafin su kwanta bacci , ga kuma labaru masu sanya nishaɗi da yake bata har bacci ya ɗauke ta ,bata zuwa ko'ina daga ɗakin ɗan liti da yake daga wajen filin rawa sai cikin gidan madam saly da take aikin wanke-wanke kofuna tare da farantan aikin burkutu tsawon yini a cikin gidan , bata da wata matsala saboda duk lokacin da yakaka ta ɗan zagaya zata taho bakin fanfon da take zaune din-din a gefen sa ta shafi kan ta koh kuwa fuskar ta , ta kuma tambaye ta bata da wata matsala koh ? Nan zata amsa mata cikin farin ciki da ita bata da wata matsala , Haka zata sake komawa bakin aikin ta tana mai farin cikin sauyin rayuwar da suka samu , musamman farin cikin da take hangowa a fuskar ƙanwar ta wacce ɗan liti ya wadata ta da ƴan kayayyakin gonjo na ƴan matasan yara maza sa'annin ta fes-fes da ita hasken ƴar luwai ɗin fatar ta ruwan zuma yana bayyanuwa, Ranar da suka kwana huɗu a gidan ɗan liti yayi mata kyautar kayan wanda daga ita har falmata kyautar bata wani faranta musu ba , saboda ƴan rigunan basu da wani girma kayan turawa ne , su kuma sun san kayan nan burguza burguza da falmata ke sanye da su sune rufin asirin su a kasantuwar falmata namiji saboda kayan ya boye ɗan tudun kirjin falmatan wanda suka fara tasowa tare da bunƙasa ,  Da kƴar yakaka ta shawo kan falmata wacce da farko ta tubure akan shawarar da yakaka ta kawo na falmatan ta dunga sanya riguna biyu bayan ta tamke kirjin ta da ɗankwali ,saboda boye tudun tare da yi mata gargaɗi kada ta yadda ta sauya kaya a gaban ɗanliti duk juyin duniya , ta kan ce     Kiyi hakuri falmata har mu ɗan tara abun da muka tara anan ɗin zuwa lokacin kuma mun san gari sosai idan ya so sai mu koma wani wurin da babu ƴan iska mu raɓa ki koma saka kayan mu na mata , kamar kowacce mace ina nan ina ware miki kayan ki cikin kayan da nake samu ," Ranar da ta fara ɗaure kirjin ta yini tayi tana fama da ciwon kirjin , amma da ta kwana biyu sai ta saba ta daina jin ciwon , Bata taɓa yin wanka sai sun tabbatar da ɗan liti ya bar da'irar wajen sannan zata yi wankan a gurguje yakaka ta raka ta ta sauya kaya tare da sake gyara mata ɗaurin kirjin ta wanda ya taimaka ƙwarai wurin boye halittun kirjin ta , sai dai salon takun tafiyar ta tare da tudun bayan ta ke sa samy baby tana yawan tsokanar ta da "Kachallah me jikin mata ,"    tafiyar ka sai kace ta hamshaƙan mata , koh kuwa tace shege kachallah da kai mace ne da anyi manyan kaya a wurin ka ," Idan yagana tana wurin tayi ta sheƙa dariya ,wacce ita ma a yanzu sha'awar rayuwar su yakakan take , domin kuwa har kuɗi da suturu yakaka ta bata daga cikin wanda samy baby ta bata ," Haka kwanaki suka yi ta tafiya har suka samu wata guda da ƴan kwanaki a dafdalar wannan gidan , wanda zuwa lokacin yakaka tayi jazur wannan maɗaukakin hasken fatar ta ta ya sake bayyana dal tamkar fitila haka take a waje , ƴar kyakkyawar ƙaramar budurwa mai sanyi tare da yawan fara'a koyaushe cikin murmushi take , ko magana yakaka take haka zaka ga fuskar ta da yalwatattacen murmushi dasashin ta a waje , wanda hakan yake tasiri matuƙa wurin bayyana ƴan ƙananun kyaun ta wanda hasken da take da shi ya fi jaan hankalin mazan da suka fara ƙaraƙaina akan ta fiye da kyan nata ," Zuwa lokacin samy baby ta fara jaan ɗamarar wanke yakaka daga dauɗar datti gami da ƙazantar ƙauye a cewar ta yakaka haja ce me matuƙar tsada , wacce sayan ta sai alhajin da ya rufu ya tada kai , " sai ya so zama tamkar gasa a tsakanin ta da madam saly wacce ita ma take bada sumfurin tata kulawar ga yakaka domin ta farga gaba kaɗan yakakan zata zame mata hanyar samun arziki ,dan haka ta fara kokarin janye ta daga wurin samy baby da ta lura tana son kawo mata tsaiko domin kuwa ga alama so take ta fanɗarar da yakaka ta sanar da ita daɗin ƴancin kai kamar yadda ita take da nata ƴancin a hannu domin samy baby ba'a ƙarƙashin kowa take ba cikin magajiyoyin gidan , da karfin ta ta shigo bariki da kuma nawin aljihunta tare da gatan ta domin ba kukan yunwa koh na rashin wurin kwana koh kuwa na neman kuɗin zuwa asibiti zubda ciki ne suka kawo ta bariki ba , ƴar cikin ƙwaryar gari ce da gatan ta da kome iyayen ta ma manyan mutane ne sanannu , uwa uba bata da duhun jahilci domin kwalin digiri ke gare ta ," sha'awar rayuwar barikin take tare da taimakon matar uban ta wacce take sake ingiza ta , uwa uba shaiɗan da yake tsakiyar kan ta yana buga ganga , Gidan kakaf ba wata tsohuwar kilaki da take shakka , sai ma su da idan jarabar su ta busa sigari koh afa ƙwayoyi suka motsa , kuma suka laluba lalitar su suka ji wayam , su je wurin ta neman ƴan kuɗaɗe sanin da suka yi kaf cikin karuwan gidan ba wacce ta kai ta kama kuɗi , da kuma kyauta domin hannun ta a sake yake bata da rowa ," Ranar wata litinin da safe yakaka ta wayi gari da wani irin matsanancin ciwon mara wanda tun kwanaki biyu da suka wuce take jin sa kaɗan kaɗan amma ta daure , Har zuwa yanzu da take kan hanyar ta ta zuwa ɗakin samy baby domin ta gyara mata ɗakin ,bayan ta gama kintsa na madam saly kamar yadda ta saba kafin su duƙufa aikin sana'ar su ," A dudduƙe da jaan ƙafa ta ƙarasa cikin ɗakin samy wacce take kwance tana sharar bacci daga ita sai ƴar ficiciyar rigar bacci kan gadon duk a hargitse kayayyakin ta tun daga kan rigar mama da ɗan kafai duk a wurge a kan gadon , tayi ɗai-ɗai da kafafu gashin dokin da yake kan ta ya baje akan filon da tayi matashin kai da shi ," idan da sabo yakaka ta saba tadda ta a haka kullum . Tana shiga ɗakin ta zube akan shimfiɗar kafet ɗin ta kwanta gami da dunƙulewa wuri guda tana murƙususu , dunƙulewar da tayi ta haɗe guiwar kafafun ta da kirjin ta sai ya sa taji rangwamen kartawa tare da murɗar da marar ta ke mata har ɗan wani bacci ta fara ji yana figarta saboda rashin bacci da tayi daren jiya a sakamakon ciwon cikin ," bata ankara ba bacci mai karfi ya fisge ta , ta sake jiki sosai tana baccin ta , Samy baby ce ta farka bayan da taji baccin ya soma gundurar ta , ta daina jin dadin sa , doguwar hamma ta hangame baki ta jaa babu neman tsari daga shaiɗan babu salati , ta gantsare bayan ta ya bada sautin ƙaƙas , tana zira ƙafar ta ƙasa ta sauke akan yakaka wacce baccin ta yake kai mata karo har tsibirin keemala na ƙasar bankok,"     Da farko ta firgita da ganin mutum kwance a gaban gadon ta sai dai fahimtar wacece a kwance ya sa ta ƙewaye ta gami da nufar kofar banɗakin da take ta cikin ɗakin nata , a ranta tana raya cewa gajiyar aiki da rashin bacci ne suka sa yakaka ta bingire anan ta na bacci , tare da sake aiyana niyyar taimakon yakakan har ta samu karfin tsayuwa da kafafun ta muddin yakakan zata yadda ta bi hanyar da zata ɗora ta ," yo ina ma zata ƙi ?? Ai duk wanda ruwa ya ci shi idan aka miƙa masa takobi sai ya kama ,"    A firgice yakaka ta farka lokacin da samy baby take tashin ta , "cikin inda-inda ta fara bata haƙuri bayan ta gaishe ta,  tare da faɗa mata cikin ta ne yake ciwo amma yanzu ya lafa ,"ta daina jin ciwon sa sosai , sai dai lema-lemar da take ji ta ƙasan ta ya sa ta gaza miƙewa sai faman muskuɗawa take cikin ran ta tana Allah ya sa dai ba fitsarin kwance tayi ba , toh amma ai ita bata fitsarin kwance tun da ƙuruciyar ta bare yanzu da ta zama ƴar budurwa , Tunanin ta ya katse lokacin da samy baby tayi mata umarni bayan ta miƙa mata kuɗi akan ta sayo mata soyayyar   indomi da ƙwai tare da shayi haɗin murtuku ya ji sugar sosai ," A sanyaye yakaka ta miƙa hannu biyu ta ƙarba tana mai taraddadin tashi kar samy baby ta ga yadda ta jiƙa mata kafet ," amma ba yadda ta iya haka ta miƙe tare da nufar bakin kofa Bin bayan ta da kallo samy baby tayi tana tunanin me ya sanyayar mata da jiki ?ko cikin ke damun ta saboda ta san a wurin aiki da aike yakaka bata da sanya ," karaf idanun ta suka sauka a bayan yakaka inda shuɗin siket ɗin yadin da take sanya da shi duk ya baci ,"   Ke yaks dawo nan wai ke me yasa kin cika gidadanci ne ?? Yanzu har yau baki yi wayewar da zaki saka pad a jikin ki idan kina menses ba ? Haba mana yaks meyasa kullum ina kai ki kina dawowa , yanzu ba dan na gani na ƙira ki ba da kenan haka zaki fita ?? Ta ƙarasa zancen tana balla mata harara ," Ƙasa da kan ta yakaka tayi tana me satar kallon wurin da ta tashi domin ita duk bata wani gane kalmar pad da menses ba , ga zaton ta faɗa samy baby take yi mata akan fitsarin da ta saddaƙar shi tayi a kwance "ɓacin rana" , sai dai ga mamakin ta wurin da ta tashin ɗan alamun danshin kaɗan ne kuma bai wani fidda kala ba saboda kafet ɗin ruwan kunkumadi ne ita ma da kƴar ta hango danshin toh akan me samy baby take mata faɗa ?? Tunanin ta ya katse lokacin da ta ji samy baby ta ce ,"       Ki buɗe ƙaramin akwati na ki ɗauki sabon pant da pad ki shiga banɗaki ki gyara jikin ki nan gaba kar ki sake zama babu pad alhalin kin san lokacin yin menses ɗin ki yayi kusa kina jin alamar sa ki tanadi pad idan ma baki da ita ki zo na baki koh kuma ki yi ƙunzugu da tsabatatatcen tsunma kin ji koh ,?? Da sauri yakaka ta gyaɗa kai tana rarraba idanu , domin ita har ga Allah ba wani fahimtar dogon bayanin samy baby tayi ba , koh ta so fahimta ma kalmomin da ta jefo guda uku da turanci sun hana ta gane kan maganar , dan haka kawai sai ta je ta durƙusa a gaban akwatin tayi zugui ," Fahimtar da samy baby tayi yakaka fa bata fahimce ta ba ya sa ta tashi ta zo ta buɗe akwatun ta tare da ciro sabon pant fil sai tashin ƙamshi yake  ( ku sani mata tsabtace undies tare da wanke shi da kuma goge shi wani babban sirri ne na sanya nishaɗi a gangar jiki tare da bada kariya na musamman daga kamuwa da cututtukan da suke addabar mata daga ƙasan su a zamanin yanzu ,ki kasance kullum cikin wanke tare da goge panties ɗin ki bayan kin shanya su a rana sun yi a ƙalla awanni shidda a rana ) da kuma ledar pad mai guda takwas ta danƙa mata," ki shiga banɗaki ki gyara jikin ki ," Da sauri yakaka ta amsa da toh ,    Kin iya amfani da shi koh ?    Gƴaɗa kai ta yi sai kuma ta sake girgiza shi ," Samy baby wacce ta fara zowa wuya da gidadanci tare da jahilcin yakaka tace ,"     Buɗe baki zaki yi kiyi magana ba ki dunga gƴaɗa min kai ya kadangaren gobara ba , kin iya amfani da shi koh na gwada miki ??    A sanyaye ta amsa ban iya ba ," Karɓa tayi tare da nuna mata yadda ake amfani da shi ta ɗora mata da ,"ki wanke siket ɗin naki a banɗakin zan miko miki wasu kayan ," Ƙiris ya rage yakaka ta kurma ihu lokacin da ta ga yadda jikin ta ya ɓaci da jini ,"tashin hankali na shiga uku na lalace fitsarin jini na fara shikenan nima zan mutu na bi su abba wayyo Allah falmata waye zai kula min da ke ,"  wannan shine tunanin da yakaka take yi lokacin da take wanke jikin ta da kayan ta , tana yi tana sharar hawaye ," Ido jazur ta fito bayan ta shirya kan ta cikin kayan da samy baby ta miƙa mata na wata koriyar atamfa riga da siket , sun zauna mata ɗas kasancewar ita ma samy baby ƴar madaidaiciya ce tamkar ta ," Sumi-sumi ta wuce tana share guntun hawaye ta nufi wurin aiken da aka mata ,' samy baby ta bi bayan ta da kallo tana me jin tausayin yarinyar na zaunawa cikin ranta , ta fahimci yau ne ta fara tsintar kan ta a yanayi na al'ada saboda tashin hankali da damuwar da ta gani tare da yakakar wanda ba kome ya jawo hakan ba illa jahilcin addini da na boko saboda da tana zuwa makaranta kowacce daga cikin ta boko koh ta islamiyya a shekarun ta da take sha shidda da ƴan watanni ya ci ace ta san me wannan jinin yake nufi saboda ana wayar da kai a makarantu ," nan take ta ji tana son tayi yunƙuri domin ganin yakaka ta ɗan samu ilmi ko kaɗan ne domin ita kan ta harkar da take son ɗora ta akai idan kana da ilmin boko kafi samun kasuwa wurin manyan wayayyun mutane irin wanda take yi wa yakakar yangen su , domin su basu cika harka da jahila ba ," zamani ya zo da kome zaka yi domin cigaban kan ka sai kana da ilmin zamani ilmi shine gishirin rayuwa ," Tana tafiya tana rarrakaɓewa ta jikin gini tafiyar kan ta ba yadda ta saba take yin ta ba tana tafe tana mammatse kafafu domin ji da take tamkar ƴar audugar da take jikin ta zata faɗo wacce rashin sanya ta a dai-dai ya sa take jin hakan ," cikin ranta kuwa kalmomin wasiyyar da zata barwa falmata take haɗawa ," Yaks baby , yaks baby , ke yaks ji mana wai yane ina miki magana kina wani ƙara wuta tamkar baki ji na , zo mana magana za muyi ," Muryar babasho mai sayar da wiski da su matallah , zuwa kan taba sigari da sauran kwayoyin sanya maye a cikin ɗan shagon da yayi da tsoffin kwanukan rufi da katako ,ta katse mata tunani , babasho yayi masifar maƙalewa yakaka , yana bala'in son ta kamar zai yi hauka ,sai dai samy baby ta kasa ta tsare ta hana ya samu damar koh ɗan zantawa da yaks , duk kuwa da cewa kullum sai ya je rumfar saly baby ya sai burkutu dan kawai ya samu ya ga fuskar yaks ," samy baby ta kan faɗa mata ," ta wuce ajin babasho fintinkau , me zata yi da wannan sauran tabar ? Da duka-duka idan aka haɗa jarinsa da shagon nasa ba zai fice dubu goma ba ,??  Ai sama tayi wa yaro nisa tsakanin ta da ire-iren su babasho sai dai ta kira su ta aike su ,"amma ita kalar manya ce kalar hamshaƙan da suka ci suka tada kai da naira , ," kar ki kuskura ki kula shi yaks bashi ma da isasshen hankali idan ya sha ta kai masa karo yana iya shaƙe ki ya kar ki ya kar banza atoh kiyi hankali," Ga yakaka kuwa ita ba ma babasho ba da take jin mugun-tsoron sa saboda chukurkuɗaɗɗan gashin sa da ya tara akai baya wani kula da shi duguzum-duguzum ya fenta kan kalar jaa shuɗi da kuma yalo , uwa uba faranta hannunsa zaƙo-zaƙo da suke cike taf da annakiyar dauɗa suna tsorata ta har su sanya ta hasashen yadda zai kafa mata farce a wuya idan ya shaƙo ta kamar yadda samy baby take faɗa mata , ita gaba ɗaya maza ma ƙarƙashin ranta tsoron su take , babu wani ɗa namiji da ta taɓa jin sa cikin ranta idan aka ɗauke dakta hamza wanda shi ma ta ɗauki tunanin sa da yake faɗo mata jifa-jifa a zuwan tana tuna sa ne domin taimakon da yayi a gare su ita da ƙanwar ta , bayan shi babu wani ɗa namiji da yakaka take ɗaga kai ta dube shi iyakar ta da su harkar cinikayyar su ta burkutu su , su zo saya ta je ta kawo musu ta karbi kuɗin ," bata taɓa buɗe baki tayi tsiwa koh rashin kunya ga kowa ba duk kuwa da yadda suke kai mata wawura tare da maganganun banza da ita bata ma kai ga fahimtar wasu kalmomin su na batsa ba ,"ita dai ba'a raba fuskar ta da tsadadden murmushin ta , dan haka yanzu ma da babasho yake kwala mata kira koh kallo bai isheta ba haka ta cigaba da tafiyar ta ,' shi kuwa ya bi bayan ta da kallo yana lashe leɓe tare da lanƙwasa ƴan yatsun sa cikin ransa yana fatan Allah ya kai damo ga harawa koh bai ci ba yayi birgima,", Karo taji tayi da mutum wanda zurfin da tayi a tunanin ta ya sa bata ga tahowar sa ba ," da sauri tayi baya ,tare da durƙusawa ta ɗauko masa makullin motar sa da ya faɗi a hannun sa ta sanya bakin gyalen ta ta goge ƙasan jikin ɗan makullin bakin ta ɗauke da kalmar ban hakuri ta miƙa masa mukullin ba tare da ta ɗago kan ta ba ,      Miƙa wankakken hannunsa mai ɗauke da wankakkun fararen farata ƙal yayi ya karbi makullin agogon hannun sa na ta ɗaukar ido ,"hannun ta bi da kallo wanda kyaun sa da gogewar sa a tsafta irin wanda bata taɓa gani ba ya ɗauke hankalin ta , muryar sa ce ta dawo da ita daga shagalal da tayi cikin hausar sa ta bamarɗe yace ,"   ", Ai ni ke da laifin ina gaugawa ban lura da ke ba yi mini afouwa ," Da hanzari ta ɗago kan ta jin muryar sa da ta yi kamar ta san ta , tana ɗagowa yana gifta ta sai tashin mabuwayin ƙamshin sa da ta shaƙa wanda ya sa ta jin tsaftar sa ta burge ta har ta waiwaya tana bin takun sa da kallo ," Har ta je ta amso aiken da aka mata tana jin ƙamshin turaren sa cike taf da hancin ta ," bayan samy baby ta ci indomie da soyayyen ƙwai ta cika cikin ta har ta barwa yakaka sauran ta cinye tas tare da wanke kwanon , ta tashi da niyyar fara gyaran ɗakin , samy baby ta dakatar da ita tare da cewa ta bata hankalin ta ," nan tayi mata bayanin jinin haila da ta fara da yadda ake wankan sa , ta kuma jaa kunnen ta akan ta kula kar ta yadda wani ɗa namiji ya ɗirka mata ciki kar ma ta kula kowa a yanzu idan lokacin fara harkar ta yayi ita da kan ta zata kaita a bata maganin hana ɗaukar ciki ta yadda zata ji daɗin cin kasuwar ta ba tare da wata fargabar yin ciki ba , nan dai suka ɗauki lokaci samy baby tana mata huɗuba wanda mafi yawan su ba na kirki bane , idan aka cire wankan hailar da ta koya mata a taƙaice babu wani abun kirki cikin sauran shawarwarin da ta bata ,'    Ki lura da kyau da lissafin kwanakin menses ɗin ki domin ta haka ne idan kin fara harka zaki gane lokacin da kike danger ɗin ki dan ki kiyaye harka a waɗannan kwanakin duk da dak zamu je a miki ƴan dabaru amma kau da bara sai ana haɗawa da zamiya ,"kin ga yau ɗaya ga wata kika fara duk inda wata ya kai shidda  takwas zuwa goma zaki iya gamawa toh kwanaki bakwai da zasu biyo bayan kwana uku na kammala jinin al'adar ki sune ranaku mafi hatsari gare ki idan kin fara harka domin tabbas kina iya samun ciki idan kika sake kika yi koh da wasa da lawurjen namiji ne ehee ,sai ki kiyaye kin ji koh ? Ba tare da yakaka ta fahimci mafi akasarin bayanan samy baby ba ta amsa da "toh" hankalin ta ya fi karkata ga son sanin wacce harka ce zata ɗora ta akai wacce har akwaj hatsarin samun ciki ?? Ita fa tana tsoron zancen ciki kowacce irin harka ce zata iya hakura da ita idan har zata iya yin ciki , toh amma tayaya ma ake samun cikin ?????? ( ta miƙa tambayar ga masu karatu 😂) Cikin sanyin jiki ta koma bakin aikin ta inda duk take a takure domin gani take kamar kowa ya san tana fitsarin jini bini-bini ta leƙa ta kalli bayan siket ɗin ta ,kou kuwa ta shiga bayi tayi tsarki , duk a matse take jin kan ta , sai dai tata damuwar ta kau koh kuwa ace ganin damuwa kwance ɓaro-ɓaro akan fuskar falmata ya sa ta daina jin ta ta sai wani sabon tashin hankali tare da damuwar da ta fi ta farko da taji ya mamaye ta , sam bata ƙaunar ganin falmata cikin damuwa   Falmata nah ! faɗa min menene ?? wani ne ya zage ki ? Koh baki da lafiya ne , yunwa kike ji ?? Koh kina son wani abu ne ?? Koh jiya ɗan liti ya miki wani abun da ya ɓata miki rai ne  ? Gaya min dan Allah menene     Ɗan guntun murmushin da daga ganin sa na ƙaƙale ne shi falmata ta ɗora a fuskar ta ,"     Yakaka ni babu wanda ya min kome kuma lafiyata ƙalau , bana  jin yunwa ,"       Toh meye ne koh kin tuno da su mama ne ??    Da sauri falmata ta gƴaɗa kai tana me rushewa da kukan da tuntuni yake cin ta , sakamakon abun da ya faru da ita a wurin wani mutum wanda ɗan liti ya ɗauke ta jiya ya kai ta a matsayin shine ubanɗakin sa wanda yake bashi kayan daɗin da yake kawo mata tana cika cikin ta da shi ," Ita dai bata san ina ɗan litin ya kai ta ba domin a mota suka tafi ,    Duk da cewa ba gani take ba amma ta fahimci gidan da ɗan liti ya kai ta gidan me hali ne , domin maɗaukakin sanyin da ta ji a parlour da suka tadda mutumin har zuwa kan lallausar abun da aka zaunar da ita akai kujera zata kira abun koh gado ?? Ita dai bata taɓa zama a makamancin abu mai taushin sa ba ga wani fitinannen ƙamshi da ya cika wurin , bata ji ta fara tsorata ba sai da ɗan liti ya ɗibo wani abu mai matsanancin sanyi ya cusa mata a baki da ya umarce ta da ta buɗe bakin ta zai bata wani abu wai shi "ice cream" anan ta ji ta tsorata domin kuwa dawo da abun tayi ta tofar da shi saboda bata taɓa shan abu mai tsananin sanyin irin sa ba ,"    Mutumin da suka tara a falon ya buɗe ƙatuwar muryar sa marar daɗin sauti kamar fasasshiyar  gangar  ya dunga tuntsira dariya ɗan liti yana taya sa harda shewa ,"     Watau kachallah bai taɓa shan ice cream ba ?? Ai kuwa daɗi ya bar ka , toh liti bashi gasasshiyar kaza ya ci nasan dai koh daga kan dutse ya sauko ya san nama , Wata ƙatuwar cinya ɗan liti ya fisgo ya damƙawa falmata a hannun ta bayan ya miƙa mata kwalin lemun ,"five alive" a ɗaya hannun ,     Maza ɗan kachallari ci kaza ka sha lemu yaro ai ka zo gidan arziki duk wasu kayan daɗi da nake kai maka kana ci kana lashe baki "ya tsohon kare nan ne tushen sa kaɗan ne daga cikin ire-iren kayan maƙulashen da suke jibge a gidan nan yaro saki jiki ka ci arziki ka bar shi a inda ka gan shi ,"     Cikin sanyin jiki falmata ta kai cinyar kazar bakin ta ta gutsuri kaɗan tana taunawa ," zaƙin kayayyakin ɗanɗano irin na alfarma tare da zaƙin naman kazar suka haɗu suka sa kunnen falmata motsi har bata san lokacin da ta cinye wacce ɗan liti ya bata ba ,     tana tanɗe baki ,  ɗan liti wanda suke kus-kus da wannan ɗan tsurut ɗin mutumin shi ya lura da ita ya sake fisgo ɗaya cinyar ya ɗangwala mata a hannu ,"       ungo maza cinye har ƙashin ka tauna ka haɗiye , yau ta shiga ranakun tarihi a wurin ka ɗan kachallari ," Miƙewa ɗan liti yayi bayan sun gama kitsa abun da suka kitsa ,"     Ɗan kachallari ni zan ɗan je na dawo nan kusa ka jira...    Koh kafin ya ƙarasa abun da yake nufin cewa falmata ta miƙe zuruf ta dangwarar da sauran naman hannun ta '',       Ah ah mu tafi tare nima zan bika ," Haɗa ido ɗan liti da wannan mutumin suka yi , mutumin ya yiwa ɗan liti alama da ido akan ya tafi kawai zasu yi waya ,"    Saɗaf-saɗaf ɗan liti ya fita ya jaa musu kofar wanda ƙarar rufe kofar ya sa falmata wacce take tsaye tana jiran amsar ɗan liti ta farga da barin ɗan liti wajen ,"      Kuka ta sa tare da fara taku tana nufar hanyar da ta ji motsin rufowar kofar da ɗan liti yayi lokaci ɗaya tana jera kiran sunan ɗan litin ,"   Dariya ta ji mutumin ya kwashe da ita  kafin ta ji ya fara tahowa inda take yana cewa haba ɗan kyakkyawan yaro kachalla menene abun kuka yi shiru yanzu ɗan liti zai dawo aiken sa nayi , kafin ya dawo zo muyi wasa ,"kafin ta ankara ta ji ya sure ta sama yana cewa ," A ɗaga sama anyi wa wada kwace 😂 ,"   Na so na baku ya fi haka , sai dai yawan cewa kuna jira da kuke yi , yasa na dakata anan kuyi manage da wannan sai mun hadu a shafi na gaba cikin yardar Ubangiji," A kan karo mutunci #umm'muaz #vote #comments #share with your Family and friends.Cikin sati biyu da tarewar su yakaka a gidan madam saly ,sun zama ƴan gari a da'irar ta yadda yakaka ta san ɗakunan manyan kilakai da ƙananun karuwan da suke unguwar saboda aiken ta da madam saly take wurin su , a gefe ɗaya kuma ta zama ƴar ɗakin samy baby , wacce bayan dawowar yakaka gidan madam saly ta gama nazarin yarinyar tsaf , ta gane bata san ma mai kalmar bariki take nufi ba kamar yadda da tayi zaton yakakar ƙaramar karuwa ce , sai ta fahimci ashe yakakan neman abun sawa a bakin salati take tare da wajen da zata sanya haƙarƙarin ta , dan haka sai ta jaa ta a jiki ta maida ta mai gyara mata ɗaki tare da yi mata ƴan kananun aike da aiki , ita kuma tana bata ƴan kuɗaɗe bayan jibgin suturun ta da ta fitar ta bata kwance , tun yakakan tana ɗari-ɗari ganin abun da samy baby tayi mata a farkon haɗuwar su , har dai ta zo ta saki jiki da ita , sosai take kyautatawa samy baby da ta riƙa a matsayin uwarɗakin ta , wacce take samun alheri tare da sakewa a wurin ta, domin a lokuta da dama har ƴar hira samy baby take zama su yi da yaks , Aikin gidan madam saly kuwa tuƙuru yakaka take yin sa domin gwanintar da take nunawa ya faranta ran madam saly da take ganin ta a matsayin ginshiƙin su cikin duniya a yanzu , bata da wani lokaci nata na kan ta sai na aikin burkutu wanda ba'a sanya ba ma yi take kamar su wanke dawa , juya ruwan dahuwar burkutun da kuma tace shi wanke kayan madam saly da gyara mata ɗaki , tun safe idan ta kama aiki sai dare karfe sha ɗaya take samun hutu ," wanda hakan ke matuƙar farantawa madam saly rai har take ganin wautar kan ta da farko,  da ta so korar su ashe dai maganar ɗan liti dutse , Ga falmata ma sai sam barka domin kuwa har ɗan kumatu tayi ta sake mul-mul , sakamakon cika mata ƙundu da ɗan liti yake da cimar daɗi kullum dare kafin su kwanta bacci , ga kuma labaru masu sanya nishaɗi da yake bata har bacci ya ɗauke ta ,bata zuwa ko'ina daga ɗakin ɗan liti da yake daga wajen filin rawa sai cikin gidan madam saly da take aikin wanke-wanke kofuna tare da farantan aikin burkutu tsawon yini a cikin gidan , bata da wata matsala saboda duk lokacin da yakaka ta ɗan zagaya zata taho bakin fanfon da take zaune din-din a gefen sa ta shafi kan ta koh kuwa fuskar ta , ta kuma tambaye ta bata da wata matsala koh ? Nan zata amsa mata cikin farin ciki da ita bata da wata matsala , Haka zata sake komawa bakin aikin ta tana mai farin cikin sauyin rayuwar da suka samu , musamman farin cikin da take hangowa a fuskar ƙanwar ta wacce ɗan liti ya wadata ta da ƴan kayayyakin gonjo na ƴan matasan yara maza sa'annin ta fes-fes da ita hasken ƴar luwai ɗin fatar ta ruwan zuma yana bayyanuwa, Ranar da suka kwana huɗu a gidan ɗan liti yayi mata kyautar kayan wanda daga ita har falmata kyautar bata wani faranta musu ba , saboda ƴan rigunan basu da wani girma kayan turawa ne , su kuma sun san kayan nan burguza burguza da falmata ke sanye da su sune rufin asirin su a kasantuwar falmata namiji saboda kayan ya boye ɗan tudun kirjin falmatan wanda suka fara tasowa tare da bunƙasa ,  Da kƴar yakaka ta shawo kan falmata wacce da farko ta tubure akan shawarar da yakaka ta kawo na falmatan ta dunga sanya riguna biyu bayan ta tamke kirjin ta da ɗankwali ,saboda boye tudun tare da yi mata gargaɗi kada ta yadda ta sauya kaya a gaban ɗanliti duk juyin duniya , ta kan ce     Kiyi hakuri falmata har mu ɗan tara abun da muka tara anan ɗin zuwa lokacin kuma mun san gari sosai idan ya so sai mu koma wani wurin da babu ƴan iska mu raɓa ki koma saka kayan mu na mata , kamar kowacce mace ina nan ina ware miki kayan ki cikin kayan da nake samu ," Ranar da ta fara ɗaure kirjin ta yini tayi tana fama da ciwon kirjin , amma da ta kwana biyu sai ta saba ta daina jin ciwon , Bata taɓa yin wanka sai sun tabbatar da ɗan liti ya bar da'irar wajen sannan zata yi wankan a gurguje yakaka ta raka ta ta sauya kaya tare da sake gyara mata ɗaurin kirjin ta wanda ya taimaka ƙwarai wurin boye halittun kirjin ta , sai dai salon takun tafiyar ta tare da tudun bayan ta ke sa samy baby tana yawan tsokanar ta da "Kachallah me jikin mata ,"    tafiyar ka sai kace ta hamshaƙan mata , koh kuwa tace shege kachallah da kai mace ne da anyi manyan kaya a wurin ka ," Idan yagana tana wurin tayi ta sheƙa dariya ,wacce ita ma a yanzu sha'awar rayuwar su yakakan take , domin kuwa har kuɗi da suturu yakaka ta bata daga cikin wanda samy baby ta bata ," Haka kwanaki suka yi ta tafiya har suka samu wata guda da ƴan kwanaki a dafdalar wannan gidan , wanda zuwa lokacin yakaka tayi jazur wannan maɗaukakin hasken fatar ta ta ya sake bayyana dal tamkar fitila haka take a waje , ƴar kyakkyawar ƙaramar budurwa mai sanyi tare da yawan fara'a koyaushe cikin murmushi take , ko magana yakaka take haka zaka ga fuskar ta da yalwatattacen murmushi dasashin ta a waje , wanda hakan yake tasiri matuƙa wurin bayyana ƴan ƙananun kyaun ta wanda hasken da take da shi ya fi jaan hankalin mazan da suka fara ƙaraƙaina akan ta fiye da kyan nata ," Zuwa lokacin samy baby ta fara jaan ɗamarar wanke yakaka daga dauɗar datti gami da ƙazantar ƙauye a cewar ta yakaka haja ce me matuƙar tsada , wacce sayan ta sai alhajin da ya rufu ya tada kai , " sai ya so zama tamkar gasa a tsakanin ta da madam saly wacce ita ma take bada sumfurin tata kulawar ga yakaka domin ta farga gaba kaɗan yakakan zata zame mata hanyar samun arziki ,dan haka ta fara kokarin janye ta daga wurin samy baby da ta lura tana son kawo mata tsaiko domin kuwa ga alama so take ta fanɗarar da yakaka ta sanar da ita daɗin ƴancin kai kamar yadda ita take da nata ƴancin a hannu domin samy baby ba'a ƙarƙashin kowa take ba cikin magajiyoyin gidan , da karfin ta ta shigo bariki da kuma nawin aljihunta tare da gatan ta domin ba kukan yunwa koh na rashin wurin kwana koh kuwa na neman kuɗin zuwa asibiti zubda ciki ne suka kawo ta bariki ba , ƴar cikin ƙwaryar gari ce da gatan ta da kome iyayen ta ma manyan mutane ne sanannu , uwa uba bata da duhun jahilci domin kwalin digiri ke gare ta ," sha'awar rayuwar barikin take tare da taimakon matar uban ta wacce take sake ingiza ta , uwa uba shaiɗan da yake tsakiyar kan ta yana buga ganga , Gidan kakaf ba wata tsohuwar kilaki da take shakka , sai ma su da idan jarabar su ta busa sigari koh afa ƙwayoyi suka motsa , kuma suka laluba lalitar su suka ji wayam , su je wurin ta neman ƴan kuɗaɗe sanin da suka yi kaf cikin karuwan gidan ba wacce ta kai ta kama kuɗi , da kuma kyauta domin hannun ta a sake yake bata da rowa ," Ranar wata litinin da safe yakaka ta wayi gari da wani irin matsanancin ciwon mara wanda tun kwanaki biyu da suka wuce take jin sa kaɗan kaɗan amma ta daure , Har zuwa yanzu da take kan hanyar ta ta zuwa ɗakin samy baby domin ta gyara mata ɗakin ,bayan ta gama kintsa na madam saly kamar yadda ta saba kafin su duƙufa aikin sana'ar su ," A dudduƙe da jaan ƙafa ta ƙarasa cikin ɗakin samy wacce take kwance tana sharar bacci daga ita sai ƴar ficiciyar rigar bacci kan gadon duk a hargitse kayayyakin ta tun daga kan rigar mama da ɗan kafai duk a wurge a kan gadon , tayi ɗai-ɗai da kafafu gashin dokin da yake kan ta ya baje akan filon da tayi matashin kai da shi ," idan da sabo yakaka ta saba tadda ta a haka kullum . Tana shiga ɗakin ta zube akan shimfiɗar kafet ɗin ta kwanta gami da dunƙulewa wuri guda tana murƙususu , dunƙulewar da tayi ta haɗe guiwar kafafun ta da kirjin ta sai ya sa taji rangwamen kartawa tare da murɗar da marar ta ke mata har ɗan wani bacci ta fara ji yana figarta saboda rashin bacci da tayi daren jiya a sakamakon ciwon cikin ," bata ankara ba bacci mai karfi ya fisge ta , ta sake jiki sosai tana baccin ta , Samy baby ce ta farka bayan da taji baccin ya soma gundurar ta , ta daina jin dadin sa , doguwar hamma ta hangame baki ta jaa babu neman tsari daga shaiɗan babu salati , ta gantsare bayan ta ya bada sautin ƙaƙas , tana zira ƙafar ta ƙasa ta sauke akan yakaka wacce baccin ta yake kai mata karo har tsibirin keemala na ƙasar bankok,"     Da farko ta firgita da ganin mutum kwance a gaban gadon ta sai dai fahimtar wacece a kwance ya sa ta ƙewaye ta gami da nufar kofar banɗakin da take ta cikin ɗakin nata , a ranta tana raya cewa gajiyar aiki da rashin bacci ne suka sa yakaka ta bingire anan ta na bacci , tare da sake aiyana niyyar taimakon yakakan har ta samu karfin tsayuwa da kafafun ta muddin yakakan zata yadda ta bi hanyar da zata ɗora ta ," yo ina ma zata ƙi ?? Ai duk wanda ruwa ya ci shi idan aka miƙa masa takobi sai ya kama ,"    A firgice yakaka ta farka lokacin da samy baby take tashin ta , "cikin inda-inda ta fara bata haƙuri bayan ta gaishe ta,  tare da faɗa mata cikin ta ne yake ciwo amma yanzu ya lafa ,"ta daina jin ciwon sa sosai , sai dai lema-lemar da take ji ta ƙasan ta ya sa ta gaza miƙewa sai faman muskuɗawa take cikin ran ta tana Allah ya sa dai ba fitsarin kwance tayi ba , toh amma ai ita bata fitsarin kwance tun da ƙuruciyar ta bare yanzu da ta zama ƴar budurwa , Tunanin ta ya katse lokacin da samy baby tayi mata umarni bayan ta miƙa mata kuɗi akan ta sayo mata soyayyar   indomi da ƙwai tare da shayi haɗin murtuku ya ji sugar sosai ," A sanyaye yakaka ta miƙa hannu biyu ta ƙarba tana mai taraddadin tashi kar samy baby ta ga yadda ta jiƙa mata kafet ," amma ba yadda ta iya haka ta miƙe tare da nufar bakin kofa Bin bayan ta da kallo samy baby tayi tana tunanin me ya sanyayar mata da jiki ?ko cikin ke damun ta saboda ta san a wurin aiki da aike yakaka bata da sanya ," karaf idanun ta suka sauka a bayan yakaka inda shuɗin siket ɗin yadin da take sanya da shi duk ya baci ,"   Ke yaks dawo nan wai ke me yasa kin cika gidadanci ne ?? Yanzu har yau baki yi wayewar da zaki saka pad a jikin ki idan kina menses ba ? Haba mana yaks meyasa kullum ina kai ki kina dawowa , yanzu ba dan na gani na ƙira ki ba da kenan haka zaki fita ?? Ta ƙarasa zancen tana balla mata harara ," Ƙasa da kan ta yakaka tayi tana me satar kallon wurin da ta tashi domin ita duk bata wani gane kalmar pad da menses ba , ga zaton ta faɗa samy baby take yi mata akan fitsarin da ta saddaƙar shi tayi a kwance "ɓacin rana" , sai dai ga mamakin ta wurin da ta tashin ɗan alamun danshin kaɗan ne kuma bai wani fidda kala ba saboda kafet ɗin ruwan kunkumadi ne ita ma da kƴar ta hango danshin toh akan me samy baby take mata faɗa ?? Tunanin ta ya katse lokacin da ta ji samy baby ta ce ,"       Ki buɗe ƙaramin akwati na ki ɗauki sabon pant da pad ki shiga banɗaki ki gyara jikin ki nan gaba kar ki sake zama babu pad alhalin kin san lokacin yin menses ɗin ki yayi kusa kina jin alamar sa ki tanadi pad idan ma baki da ita ki zo na baki koh kuma ki yi ƙunzugu da tsabatatatcen tsunma kin ji koh ,?? Da sauri yakaka ta gyaɗa kai tana rarraba idanu , domin ita har ga Allah ba wani fahimtar dogon bayanin samy baby tayi ba , koh ta so fahimta ma kalmomin da ta jefo guda uku da turanci sun hana ta gane kan maganar , dan haka kawai sai ta je ta durƙusa a gaban akwatin tayi zugui ," Fahimtar da samy baby tayi yakaka fa bata fahimce ta ba ya sa ta tashi ta zo ta buɗe akwatun ta tare da ciro sabon pant fil sai tashin ƙamshi yake  ( ku sani mata tsabtace undies tare da wanke shi da kuma goge shi wani babban sirri ne na sanya nishaɗi a gangar jiki tare da bada kariya na musamman daga kamuwa da cututtukan da suke addabar mata daga ƙasan su a zamanin yanzu ,ki kasance kullum cikin wanke tare da goge panties ɗin ki bayan kin shanya su a rana sun yi a ƙalla awanni shidda a rana ) da kuma ledar pad mai guda takwas ta danƙa mata," ki shiga banɗaki ki gyara jikin ki ," Da sauri yakaka ta amsa da toh ,    Kin iya amfani da shi koh ?    Gƴaɗa kai ta yi sai kuma ta sake girgiza shi ," Samy baby wacce ta fara zowa wuya da gidadanci tare da jahilcin yakaka tace ,"     Buɗe baki zaki yi kiyi magana ba ki dunga gƴaɗa min kai ya kadangaren gobara ba , kin iya amfani da shi koh na gwada miki ??    A sanyaye ta amsa ban iya ba ," Karɓa tayi tare da nuna mata yadda ake amfani da shi ta ɗora mata da ,"ki wanke siket ɗin naki a banɗakin zan miko miki wasu kayan ," Ƙiris ya rage yakaka ta kurma ihu lokacin da ta ga yadda jikin ta ya ɓaci da jini ,"tashin hankali na shiga uku na lalace fitsarin jini na fara shikenan nima zan mutu na bi su abba wayyo Allah falmata waye zai kula min da ke ,"  wannan shine tunanin da yakaka take yi lokacin da take wanke jikin ta da kayan ta , tana yi tana sharar hawaye ," Ido jazur ta fito bayan ta shirya kan ta cikin kayan da samy baby ta miƙa mata na wata koriyar atamfa riga da siket , sun zauna mata ɗas kasancewar ita ma samy baby ƴar madaidaiciya ce tamkar ta ," Sumi-sumi ta wuce tana share guntun hawaye ta nufi wurin aiken da aka mata ,' samy baby ta bi bayan ta da kallo tana me jin tausayin yarinyar na zaunawa cikin ranta , ta fahimci yau ne ta fara tsintar kan ta a yanayi na al'ada saboda tashin hankali da damuwar da ta gani tare da yakakar wanda ba kome ya jawo hakan ba illa jahilcin addini da na boko saboda da tana zuwa makaranta kowacce daga cikin ta boko koh ta islamiyya a shekarun ta da take sha shidda da ƴan watanni ya ci ace ta san me wannan jinin yake nufi saboda ana wayar da kai a makarantu ," nan take ta ji tana son tayi yunƙuri domin ganin yakaka ta ɗan samu ilmi ko kaɗan ne domin ita kan ta harkar da take son ɗora ta akai idan kana da ilmin boko kafi samun kasuwa wurin manyan wayayyun mutane irin wanda take yi wa yakakar yangen su , domin su basu cika harka da jahila ba ," zamani ya zo da kome zaka yi domin cigaban kan ka sai kana da ilmin zamani ilmi shine gishirin rayuwa ," Tana tafiya tana rarrakaɓewa ta jikin gini tafiyar kan ta ba yadda ta saba take yin ta ba tana tafe tana mammatse kafafu domin ji da take tamkar ƴar audugar da take jikin ta zata faɗo wacce rashin sanya ta a dai-dai ya sa take jin hakan ," cikin ranta kuwa kalmomin wasiyyar da zata barwa falmata take haɗawa ," Yaks baby , yaks baby , ke yaks ji mana wai yane ina miki magana kina wani ƙara wuta tamkar baki ji na , zo mana magana za muyi ," Muryar babasho mai sayar da wiski da su matallah , zuwa kan taba sigari da sauran kwayoyin sanya maye a cikin ɗan shagon da yayi da tsoffin kwanukan rufi da katako ,ta katse mata tunani , babasho yayi masifar maƙalewa yakaka , yana bala'in son ta kamar zai yi hauka ,sai dai samy baby ta kasa ta tsare ta hana ya samu damar koh ɗan zantawa da yaks , duk kuwa da cewa kullum sai ya je rumfar saly baby ya sai burkutu dan kawai ya samu ya ga fuskar yaks ," samy baby ta kan faɗa mata ," ta wuce ajin babasho fintinkau , me zata yi da wannan sauran tabar ? Da duka-duka idan aka haɗa jarinsa da shagon nasa ba zai fice dubu goma ba ,??  Ai sama tayi wa yaro nisa tsakanin ta da ire-iren su babasho sai dai ta kira su ta aike su ,"amma ita kalar manya ce kalar hamshaƙan da suka ci suka tada kai da naira , ," kar ki kuskura ki kula shi yaks bashi ma da isasshen hankali idan ya sha ta kai masa karo yana iya shaƙe ki ya kar ki ya kar banza atoh kiyi hankali," Ga yakaka kuwa ita ba ma babasho ba da take jin mugun-tsoron sa saboda chukurkuɗaɗɗan gashin sa da ya tara akai baya wani kula da shi duguzum-duguzum ya fenta kan kalar jaa shuɗi da kuma yalo , uwa uba faranta hannunsa zaƙo-zaƙo da suke cike taf da annakiyar dauɗa suna tsorata ta har su sanya ta hasashen yadda zai kafa mata farce a wuya idan ya shaƙo ta kamar yadda samy baby take faɗa mata , ita gaba ɗaya maza ma ƙarƙashin ranta tsoron su take , babu wani ɗa namiji da ta taɓa jin sa cikin ranta idan aka ɗauke dakta hamza wanda shi ma ta ɗauki tunanin sa da yake faɗo mata jifa-jifa a zuwan tana tuna sa ne domin taimakon da yayi a gare su ita da ƙanwar ta , bayan shi babu wani ɗa namiji da yakaka take ɗaga kai ta dube shi iyakar ta da su harkar cinikayyar su ta burkutu su , su zo saya ta je ta kawo musu ta karbi kuɗin ," bata taɓa buɗe baki tayi tsiwa koh rashin kunya ga kowa ba duk kuwa da yadda suke kai mata wawura tare da maganganun banza da ita bata ma kai ga fahimtar wasu kalmomin su na batsa ba ,"ita dai ba'a raba fuskar ta da tsadadden murmushin ta , dan haka yanzu ma da babasho yake kwala mata kira koh kallo bai isheta ba haka ta cigaba da tafiyar ta ,' shi kuwa ya bi bayan ta da kallo yana lashe leɓe tare da lanƙwasa ƴan yatsun sa cikin ransa yana fatan Allah ya kai damo ga harawa koh bai ci ba yayi birgima,", Karo taji tayi da mutum wanda zurfin da tayi a tunanin ta ya sa bata ga tahowar sa ba ," da sauri tayi baya ,tare da durƙusawa ta ɗauko masa makullin motar sa da ya faɗi a hannun sa ta sanya bakin gyalen ta ta goge ƙasan jikin ɗan makullin bakin ta ɗauke da kalmar ban hakuri ta miƙa masa mukullin ba tare da ta ɗago kan ta ba ,      Miƙa wankakken hannunsa mai ɗauke da wankakkun fararen farata ƙal yayi ya karbi makullin agogon hannun sa na ta ɗaukar ido ,"hannun ta bi da kallo wanda kyaun sa da gogewar sa a tsafta irin wanda bata taɓa gani ba ya ɗauke hankalin ta , muryar sa ce ta dawo da ita daga shagalal da tayi cikin hausar sa ta bamarɗe yace ,"   ", Ai ni ke da laifin ina gaugawa ban lura da ke ba yi mini afouwa ," Da hanzari ta ɗago kan ta jin muryar sa da ta yi kamar ta san ta , tana ɗagowa yana gifta ta sai tashin mabuwayin ƙamshin sa da ta shaƙa wanda ya sa ta jin tsaftar sa ta burge ta har ta waiwaya tana bin takun sa da kallo ," Har ta je ta amso aiken da aka mata tana jin ƙamshin turaren sa cike taf da hancin ta ," bayan samy baby ta ci indomie da soyayyen ƙwai ta cika cikin ta har ta barwa yakaka sauran ta cinye tas tare da wanke kwanon , ta tashi da niyyar fara gyaran ɗakin , samy baby ta dakatar da ita tare da cewa ta bata hankalin ta ," nan tayi mata bayanin jinin haila da ta fara da yadda ake wankan sa , ta kuma jaa kunnen ta akan ta kula kar ta yadda wani ɗa namiji ya ɗirka mata ciki kar ma ta kula kowa a yanzu idan lokacin fara harkar ta yayi ita da kan ta zata kaita a bata maganin hana ɗaukar ciki ta yadda zata ji daɗin cin kasuwar ta ba tare da wata fargabar yin ciki ba , nan dai suka ɗauki lokaci samy baby tana mata huɗuba wanda mafi yawan su ba na kirki bane , idan aka cire wankan hailar da ta koya mata a taƙaice babu wani abun kirki cikin sauran shawarwarin da ta bata ,'    Ki lura da kyau da lissafin kwanakin menses ɗin ki domin ta haka ne idan kin fara harka zaki gane lokacin da kike danger ɗin ki dan ki kiyaye harka a waɗannan kwanakin duk da dak zamu je a miki ƴan dabaru amma kau da bara sai ana haɗawa da zamiya ,"kin ga yau ɗaya ga wata kika fara duk inda wata ya kai shidda  takwas zuwa goma zaki iya gamawa toh kwanaki bakwai da zasu biyo bayan kwana uku na kammala jinin al'adar ki sune ranaku mafi hatsari gare ki idan kin fara harka domin tabbas kina iya samun ciki idan kika sake kika yi koh da wasa da lawurjen namiji ne ehee ,sai ki kiyaye kin ji koh ? Ba tare da yakaka ta fahimci mafi akasarin bayanan samy baby ba ta amsa da "toh" hankalin ta ya fi karkata ga son sanin wacce harka ce zata ɗora ta akai wacce har akwaj hatsarin samun ciki ?? Ita fa tana tsoron zancen ciki kowacce irin harka ce zata iya hakura da ita idan har zata iya yin ciki , toh amma tayaya ma ake samun cikin ?????? ( ta miƙa tambayar ga masu karatu 😂) Cikin sanyin jiki ta koma bakin aikin ta inda duk take a takure domin gani take kamar kowa ya san tana fitsarin jini bini-bini ta leƙa ta kalli bayan siket ɗin ta ,kou kuwa ta shiga bayi tayi tsarki , duk a matse take jin kan ta , sai dai tata damuwar ta kau koh kuwa ace ganin damuwa kwance ɓaro-ɓaro akan fuskar falmata ya sa ta daina jin ta ta sai wani sabon tashin hankali tare da damuwar da ta fi ta farko da taji ya mamaye ta , sam bata ƙaunar ganin falmata cikin damuwa   Falmata nah ! faɗa min menene ?? wani ne ya zage ki ? Koh baki da lafiya ne , yunwa kike ji ?? Koh kina son wani abu ne ?? Koh jiya ɗan liti ya miki wani abun da ya ɓata miki rai ne  ? Gaya min dan Allah menene     Ɗan guntun murmushin da daga ganin sa na ƙaƙale ne shi falmata ta ɗora a fuskar ta ,"     Yakaka ni babu wanda ya min kome kuma lafiyata ƙalau , bana  jin yunwa ,"       Toh meye ne koh kin tuno da su mama ne ??    Da sauri falmata ta gƴaɗa kai tana me rushewa da kukan da tuntuni yake cin ta , sakamakon abun da ya faru da ita a wurin wani mutum wanda ɗan liti ya ɗauke ta jiya ya kai ta a matsayin shine ubanɗakin sa wanda yake bashi kayan daɗin da yake kawo mata tana cika cikin ta da shi ," Ita dai bata san ina ɗan litin ya kai ta ba domin a mota suka tafi ,    Duk da cewa ba gani take ba amma ta fahimci gidan da ɗan liti ya kai ta gidan me hali ne , domin maɗaukakin sanyin da ta ji a parlour da suka tadda mutumin har zuwa kan lallausar abun da aka zaunar da ita akai kujera zata kira abun koh gado ?? Ita dai bata taɓa zama a makamancin abu mai taushin sa ba ga wani fitinannen ƙamshi da ya cika wurin , bata ji ta fara tsorata ba sai da ɗan liti ya ɗibo wani abu mai matsanancin sanyi ya cusa mata a baki da ya umarce ta da ta buɗe bakin ta zai bata wani abu wai shi "ice cream" anan ta ji ta tsorata domin kuwa dawo da abun tayi ta tofar da shi saboda bata taɓa shan abu mai tsananin sanyin irin sa ba ,"    Mutumin da suka tara a falon ya buɗe ƙatuwar muryar sa marar daɗin sauti kamar fasasshiyar  gangar  ya dunga tuntsira dariya ɗan liti yana taya sa harda shewa ,"     Watau kachallah bai taɓa shan ice cream ba ?? Ai kuwa daɗi ya bar ka , toh liti bashi gasasshiyar kaza ya ci nasan dai koh daga kan dutse ya sauko ya san nama , Wata ƙatuwar cinya ɗan liti ya fisgo ya damƙawa falmata a hannun ta bayan ya miƙa mata kwalin lemun ,"five alive" a ɗaya hannun ,     Maza ɗan kachallari ci kaza ka sha lemu yaro ai ka zo gidan arziki duk wasu kayan daɗi da nake kai maka kana ci kana lashe baki "ya tsohon kare nan ne tushen sa kaɗan ne daga cikin ire-iren kayan maƙulashen da suke jibge a gidan nan yaro saki jiki ka ci arziki ka bar shi a inda ka gan shi ,"     Cikin sanyin jiki falmata ta kai cinyar kazar bakin ta ta gutsuri kaɗan tana taunawa ," zaƙin kayayyakin ɗanɗano irin na alfarma tare da zaƙin naman kazar suka haɗu suka sa kunnen falmata motsi har bata san lokacin da ta cinye wacce ɗan liti ya bata ba ,     tana tanɗe baki ,  ɗan liti wanda suke kus-kus da wannan ɗan tsurut ɗin mutumin shi ya lura da ita ya sake fisgo ɗaya cinyar ya ɗangwala mata a hannu ,"       ungo maza cinye har ƙashin ka tauna ka haɗiye , yau ta shiga ranakun tarihi a wurin ka ɗan kachallari ," Miƙewa ɗan liti yayi bayan sun gama kitsa abun da suka kitsa ,"     Ɗan kachallari ni zan ɗan je na dawo nan kusa ka jira...    Koh kafin ya ƙarasa abun da yake nufin cewa falmata ta miƙe zuruf ta dangwarar da sauran naman hannun ta '',       Ah ah mu tafi tare nima zan bika ," Haɗa ido ɗan liti da wannan mutumin suka yi , mutumin ya yiwa ɗan liti alama da ido akan ya tafi kawai zasu yi waya ,"    Saɗaf-saɗaf ɗan liti ya fita ya jaa musu kofar wanda ƙarar rufe kofar ya sa falmata wacce take tsaye tana jiran amsar ɗan liti ta farga da barin ɗan liti wajen ,"      Kuka ta sa tare da fara taku tana nufar hanyar da ta ji motsin rufowar kofar da ɗan liti yayi lokaci ɗaya tana jera kiran sunan ɗan litin ,"   Dariya ta ji mutumin ya kwashe da ita  kafin ta ji ya fara tahowa inda take yana cewa haba ɗan kyakkyawan yaro kachalla menene abun kuka yi shiru yanzu ɗan liti zai dawo aiken sa nayi , kafin ya dawo zo muyi wasa ,"kafin ta ankara ta ji ya sure ta sama yana cewa ," A ɗaga sama anyi wa wada kwace 😂 ,"   Na so na baku ya fi haka , sai dai yawan cewa kuna jira da kuke yi , yasa na dakata anan kuyi manage da wannan sai mun hadu a shafi na gaba cikin yardar Ubangiji," A kan karo mutunci #umm'muaz #vote #comments #share with your Family and friends. [6/24, 10:59 AM] +234 701 013 7848: *© Fikrah Writers Association* *MAFARI* (hargitsin rayuwa) *Umm"mu'az* *18* Tuƙuru ɗan tsamurmurin mutumin nan yake son danne falmata , sai dai lamarin ya faskara domin daga ya samu nasarar cillata kan gadon kafin yayi wani yunƙuri ta zabura ta mike , babu abun da ya fi fusata shi da har ya kai shi ga danna mata cizo a kafaɗa irin ihun da ta buɗe maƙogoro tana yi tun karfin ta , wanda hakan ba karamin tada masa da hankali yayi ba sanin da yayi matar sa tana nan a sashin ta da yake maƙotan nasa , zata iya jin ihun falmata kuma duk irin manyan alfashan da yake aikatawa matar tasa bata kai ga sanin wannan mafi muni daga cikin su ba watau ,"luwaɗi," baya kuma son ta sani domin yana matuƙar son ta bai haɗa ta da kowacce mace ba cikin rayuwar sa ita take biya masa bukatar sa uwa uba ita ce silar arzikin sa tare da bazar ta yake taka rawa ," neman yara maza da basu kai ga balaga ba da yake yi a duk daren lahadi wayewar litinin wani sirri ne cikin rayuwar sa ," Dan haka a wannan karon cikin hakin da gajiyar kokawar da yake yi ya haifar masa , gami da tsabar mugunta ya ɗaga falmata a karo na takwas ya maka ta da kan katifar gami da sanya hannun sa ya danne mata baki , ya fara ƙokarin zare mata bujen ta da ɗaya hannun ," Bai ankara ba yaji ta gantsara masa wani fitinannen cizo a ɗan yatsan sa babba , wanda hakan ya sa shi sakin wani ihun azaba jin tana yunkurin gutsire mishi ɗan yatsa ," Da ɗaya hannun sa yayi amfani wajen kai mata maruka da duka ta ko'ina amma falmata ko gizau taƙi sakin ɗan yatsan da zuwa yanzu take jin gishiri-gishiri a bakin ta da ta tabbatar jinin sa ne ," ƙara nutsa haƙoran ta tayi da ya sanya shi ba shiri ya daina dukan ta ya koma roko cikin kuka akan ta sakar masa yatsa ," Bata sakar masa da yatsan ba sai da ta tabbatar ta jikkata shi ta inda ko ta sake shi jinyar raunin da tayi masa zai fara sannan ta sakar masa yatsan ta miƙe da sauri tana tofar da jinin da ya zuba mata cikin baki," Tana sakin sa ya tashi da gudu ya buɗe kofar banɗaki da yake cikin ɗakin ,' Tana jin tashin muryar sa tare da ihu lokacin da ya buɗe fanfo yana wanke yatsan ," Bin bango ta fara yi da lalube tana neman hanyar fita duk kayan jikin ta sun yamutse , tsumman da take ɗaure kirjin ta da shi ya zazzago wanda hakan ya bawa kirjin ta damar tasowa , Sai dai duk yadda ta kai ga lalubawa ta gaza gano kofar bare ta buɗe ta sai kewayawa take yi cikin hawayen tausayin kai da take yi ," makanta mutuwar tsaye ," Ido jawur ya fito ya tsaya ta bayan ta yana kallon ta cikin ran sa yana aiyana irin azabar da zai ganawa yaron nan a daren yau ," Cigaba yayi da naɗe hannun sa da Bandage yana kallon yadda take ta laluben bango , chak ya tsaya da abun da yake lokacin da idanun sa suka fara bayyana masa ainahin surar ta ta ƴa mace ,' Sosai ya ƙura mata ido yana kare mata kallo daga sama har ƙasa domin tabbatarwa ," Wata chafka yayi mata tare da haɗa ta da bango yana mai ɗaura hannayen sa akan kirjin ta , Zabura tayi ta angaje shi baya, Dan ubanki daman ke mace ce ?? Shine aka kawo min ke a matsayin namiji ?? Kika bani wahala irin wannan har da yi min rauni ? ashe ma ungulu da kan zabo ce ? Me zanyi da macen titi ? Kuma ma ƙwaila ? Dan uban ki yau zaki yabawa aya zaƙin ta , sai na wassafa ki ta yadda gaba baza ki sake yadda ayi haɗin baki da ke ba , ƴar yarinya da ke amma har kin san ta kan bariki , kin san yadda ake maguɗi , Bugun kofar falon da aka Fara yi da karfi shi ya sa shi dakatawa da maganar da yake yi ,tare da yin kasaƙe domin sauraro , ai kuwa ya tsinkayo muryar matar sa tana danna masa kira tare da cigaba da bugun kofar , wani irin zillo yayi cikin taraddadin riskar falmata da zata yi cikin ɗakin sa ,' Diri-diri yayi yana neman abun yi ba tare da ya lura da falmata wacce ta fara kokarin kintsa kanta ta cikin shigar ta na maza ba, Bugun yana tsananta tare da ƙarin fargabar sa juyowa yayi da nufin chafkar falmata ya tura ta cikin wardrobe Ya kulle domin ya san muddin matar sa tayi ido hudu da budurwa a ɗaƙin sa da daren nan kome zai faɗa mata baza ta yadda ba , bai kuma san wanne irin mataki zata ɗauka akan sa ba , da ya san ba mai sauki bane domin ya san kalar kishin ta na masifa dan haka ya gama yanke shawarar ko ta halin ƙaƙa sai ya rufawa kan sa asiri ko da kuwa zai kashe falmata ne, Sai dai ga mamakin sa shirye ya ga falmatan tsaf yaro namiji kamar dai yadda ɗan liti ya kawo masa ita , wanda ya tabbatar a kallo ɗaya baza'a taba gane falmata ƴar budurwa bace , Wani ɗan sanyin daɗi ya ji cikin ransa , Dan haka ya matso kusa da falmatan Dan uban ki ga mata ta ta zo tana buga min kofa , idan kika yadda kika yi wani abun da ya sa ta gane ke mace ce sai na kashe ki kin ji ko baki ji ba ?? Cikin sauri falmata take gyaɗa kan ta tana gwalalo ido jin kalmar kisa daga bakin sa wanda azabar da ya gana mata a cikin mintuna da suke ƙasa da talatin ya sa ta tabbatar tsaf zai iya sheƙe ta har lahira ," Ungo nan ya watso mata kayan sa masu datti da ya ciro su daga loƙo , ki riƙe su a matsayin garƙuwar ki da zata fidda ki gidan nan lafiya Da gudu ya fita ya buɗewa matar sa da take tsaye daga bakin kofa tana ƙuta , tare da mamakin meye yake yi haka a ciki da bai jin bugun kofa kuma ta kira wayar sa bai ɗauka ba , ita ba kome ya kawo ta ba illah ihun da ta tsinkayo daga sashin nasa ," ta ɗaga hannu da nufin sake buga kofar ,karaf ya buɗo kofar Yanayin fuskar sa kawai ta duba ta san ba lafiya ba , lafiya kuwa baban sadiq? ta tambaye shi , Subahananlahi ta furta hakan tana mai riko hannun sa da ta gani naɗe da bandage kafin ta ja shi ciki tana tambayar sa cikin tashin hankali akan meye ya same shi , ' shi kuwa sai faman yamutsa fuska yake cikin alamun nuna jin zafin ciwon ," Kwantar da hankalin ki my dear ɗan ciwo na ji da wuƙa ,ya furta hakan yana me satar kallon kofar ɗakin sa cikin ransa yana zagin falmata akan me ta tsaya yi masa kuma cikin ɗaki ? Fitowar falmata rungume da kayan da ta naɗe su da kƴar cikin daya daga cikin rigunan nasa , shi ya maida hankalin matar sa kan falmata ,' Bin falmatar tayi da kallo lokacin da ta ga ta doshi jikin bango gadan-gadan tana shirin cin karo ," Kai yaro kai kuma daga ina da daren nan ? Chak falmata ta tsaya lokacin da ta ji kafar ta ta zunguri garu , Juyawa tayi ga mijin ta wanda yayi kicin-kicin da fuska , Baban sadiq kana ganin yaron da nake gani koh dai gamo nayi ? Cikin bagararwa yace wane irin gamo kuma bilkisu ? Yaro ne ya shigo karɓan kayan wanki ,? Kayan wanki kuma ? A daren nan ? Kuma naga kai kake kai kayan ka laundry da kan ka yaushe kuma ka koma bawa masu wanki , ? Tukun ma yaron baya gani ne naga yana bulunbutuwa ? Bagarar da sauran tambayoyin ta yayi ya bata amsar tambayar ta ta karshe almajiri ne kuma makaho ," nuna masa hanyar fita daga falon , ya saki ƴar wata ƙarar da ke bayyana azabar da hannun sa yake yi ,da hakan ya tilasta bilkisu ta bar sauran tambayoyin ta tare da watsar da wasi-wasin da ya fara zuwar mata na ganin yaro a turakar maigidan nata har uwar ɗaki da dare ,' Ta kama hannun falmata wacce tun da a garin neman hanya ta bige ɗan yatsan ta da kafar kujera ta raƙube ta tsaya daga wajen tana sauraran duk maganganun su ,cikin ranta ta gudurta muddin ta ga matar nan zata zalunce ta , zata fyaɗe mata biri har wutsiya ta faɗa mata gaskiyar zancen , idan ya so shi mijin nata ya kashe ta a gaban matar ta sa kamar yadda ya ce ," Ga hanya nan ka miƙe nan kar kayi kwana ,' Ɗan turus tayi cikin kokonton Kai yaro ! Chak falmata ta tsaya wacce har ta fara taku cikin sauri tare da hamdalar kubutar da ita da Allah yayi daga hannun wannan azzalumin mutumin da bata kai ga sanin sunan sa ba ," Waye ya kawo ka ? Ina nufin tare da wa kuka shigo gidan ? Unn'umm'un tare tare da alhajin muka shigo shi ya kawo ni ," cikin inda-inda kalaman suke fitowa daga bakin falmata ,' Shikenan tafi," Babu ko waiwaye falmata ta miƙa hanya , bata yi wata tafiya mai nisa ba ta fara tsinkayo tashin muryar ɗan liti da yake hira da wani , yana ta faman sheƙa dariya cikin salon maganar sa ," wata irin tsanar sa ta taso ta maƙure ta ," macuci azzalumi ta ambata a ranta ,' Hangon ta da ɗan liti yayi ya sa shi miƙewa daga inda yake zaune akan bencin mai gadi suna hirar su ta duniya domin zamu ce ta tadda muje mu ,( yaƙin ruwa ya ci sakaina ,) shi ma maigadin tsohon ɗan iska ne wanda duniya ta gama kare masa ba tare da ya farga ba , duk wasu tsiyatakun da ubangidan sa yake yi ya sani , ya kuma san ɗan liti kawalin ubangidan sa ne , dan kuwa duk lokacin da ɗan litin ya shiga da yaron da ya kawo , nan yake zama a wurin sa yayi jiran fitowar yaron ,' A ah kaga ɗan kachallarin Alhaji har ka fito ? Iyeeh har da kaya haka alhajin ya baka ,?? Inji dai baka yi masa gardama ba ?? Ka saki jiki ka ci tsokokin nama ka kora da ruwan tatattun ƴaƴan itatuwa yadda ya kamata ? Toh albishirin ka ɗan kachallari ? Kafin ka ce goro kawo kayan na riƙe maka ya furta hakan yana mai karɓe kayan hannun falmata ," Sati mai zuwa iwar haka kana nan na sake kawo ka ka dangwali arziki kayi buroshi da zuƙa-zuƙan cinyoyin kaza ɗan kachallari fiye da yadda kayi a yau,' Ni bazan sake zuwa ba , bazan sake bin ka ba , ka maida ni gida ,' falmata ta furta hakan tana me rushewa da kuka Wata ƴar iskar dariya ɗan liti ya kwashe da ita da ya sa falmata ƙaro sautin kukan ta wanda yake tabbatarwa da ɗan liti aikin gama ya gama a tunanin sa ,' Tsawon dare falmata bata yi wani baccin kirki ba daga ta fara baccin zata ji ƙarar marukan da mutumin nan ya dunga yi mata , cikin ranta tana sake tsorata da mutane gaba ɗaya , abun da ta fahimta a ɗan ƙarancin shekarun ta shine mutane basu da kirki mafi yawan su azzalumai ne tana mace bata huta ba ta zama namiji ma bata tsira ba , sai dai cikin ran ta tayi niyyar boyewa yakaka abun da ya faru da ita domin ta huttashe ta shiga damuwa a dalilin ta , tasan daga lokacin da yakaka ta ji abun da ya faru baza ta sake samun nutsuwa ba har sai ta samo hanyar da take ganin ta bada kariya a gare ta , kwatankwacin wacce ta baro su daga sansanin su , a gare ta samun kwanciyar hankali tare da walwalar da take tsinkayowa daga muryar yakaka yafi mata kome , baza ta so tayi wani abu da zai Wargaza mata farinciki ba , hakan ya sa da a halin yanzun yakaka ta takura ta faɗa mata abun da ya sa ta kuka , taƙi bayyana mata haƙiƙanin gaskiya ta danganta kukan ta da tuno da mahaifan su da tayi , Kwanaki biyun da suka biyo baya sun yi su ne cikin takura , ita yakaka al'adar da take yi ita ta hana ta sakewa a matsayin ta na sabon shiga , dan haka duk a takure take jin kan ta gani take kamar kowa ya san halin da take ciki duk kuwa da cewa dai-dai gwargawdo samy baby ta wayar mata da kai tare da saya mata sabbin pad da pants,kuma zuwa yau da take kwanaki biyar da fara yi , ya fara jaa baya, ita kuwa falmata fargabar da take danƙare cikin ran ta akan irin matakin da ɗan liti zai ɗauka akan ta ne a lokacin da mutumin da ya kai ta wajen sa ya tabbatar masa da cewa ita mace ce , Sai dai a yau da ake kwana biyar da faruwar lamarin ta ɗan samu nutsuwar zuciya ganin har yau bata ji ko ganin wani sauyin da yake nuna mutumin nan ya gayawa ɗan liti wani zance ba, dan haka ta sake suka yi hirar su ita da yakaka da yagana waɗanda suke ɗan zagayowa su taya ta wanke-wanke , walwalar ta ta sauya zuwa taraddadi ne lokacin da ta ji muryar ɗan liti yana dannanawa madam saly kira , ahayye nanayee madam saly fito, fito , fito ki ji sabon bayani abun mamaki ciyawa da cin doki ,wai kamar mu a garin nan za'a nunawa barikanci , za'a yi mana ungulu da kan zabo ,? Chafɗijam , inji masu iya magana suka ce bar ganin ƙanƙantar allura karfe ce , yekuwa jama'a ku hallaro ku ji abun al'ajabi ango ya kwana da ƙunzugu , Da ɗai-ɗaya hankali mutanen wurin ya fara dawowa kan sa saboda tsabar ƙwarmaton sa hatta masu cinikin madam saly da suke cikin rumfa sai da suka ji yo shi wasu ma har suka tsallako suka zo ganin dal ," Liti yaya ne ? Yaya ne ?ya da irin wannan kiran haka ? Ta samu ne ? Ko kuwa ta guntso ne zata fesar , ? Kunne na tarwai ina jin ka bamu mu sha ," cewar madam saly wacce take ƙarasowa wurin tare da wasu daga cikin ƴan aikin gidan ," To wallahi yaran nan yaks da ƙawar ta tare da munafiki koh munafukar ƙanwar ta zan ce ? Yo abun ne ya sauya , ninke mu baibai suka yi suka buga mana stamp ɗin sakarkaru na gaya miki, " Wani banzan kallo madam saly take sakar masa kafin ta jaa ɗan guntun tsaki , Ban gane ba ? Daman akan waɗannan yaran kake kwalla wa jama'a kira har da yekuwa ? , kai dai Allah wadaran ka dan liti Tsiya ta da ke wutar ciki madam saly , toh na rantse da Allah kachalla dai mace ce , macen ma luntsumemiya kuma nunanniya , shine dan iskanci da kuturun munafurci yaran nan suka ce wani wai namiji ne , aradun Allah ma ni ban yadda da su ba idan ba turo su ɗaukar rohoto aka yi ba , atoh ki dai bincika ki kuma san abun da kike ciki kar sai kin baje kafafu ki ji anyi ramm da ke anyi sama da duwaiwan ki atoh , zamanin nan na yanzu ko inuwar ka baka sakankance da ita ba dan zata iya harɗewa ta shige cikin na makiyin ka idan kuka jeru, ji min duniya mai abun mamaki wai ƴan waɗannan ƙuya-ƙuyan yaran sun iya dabo-dabo da rufa-rufa , toh dan uban uban ku yau asirin ku ya tonu ," Duk maganganun da yake suna sauka a kunnuwan falmata wacce take duƙe a bakin fanfo da kuma yakaka wacce ta kawo kai domin shigowa ta karbi burkutu ta kaiwa abokan ciniki , dukkanin su tsam suka yi da jin kalaman ɗan liti , wannan fa shi ake kira an yanka ta tashi , take falmata ta fara yin hawaye , yayin da yakaka ta ɗaure ta cije tare da jaan ƙwanjin kare falmata ,"sai dai ayi wacce za'a yi wai bera ya zubda garin ƙyanwa ," Madam saly ce ta juya ga falmata bayan da ta gama jin zantukan ɗan liti , Kai kachalla zo nan Sum-sum falmata ta taso tana laluben hanya ta sashin da taji tashin muryar madam saly Haiyaratataa ni idan ba makantar taki ma ban yadda da ita ba , ni daman kullum ina shakkar waɗannan idanun naki da suke wural uwa na mujiya da tsakiyar dare ace wai bakya gani ??? Cewar ɗan liti wanda yake jijjiga ya dogare daga gefe ," Kai kachallah meye gaskiyar maganar da ɗan liti yake faɗa akan ka ? Tambayar da madam saly ta jefawa falmata wacce take durƙushe a gaban ta kenan , " Madam karya yake min ni ban san kome akan abun da yake cewa ba ," Wata irin zaburowa ɗan liti yayi ya dako tsalle ya bangaje ƴan matan da suke tsaye daga gaban shi ,ya dire a gaban falmata ," Dan ubanki Alhaji basko zai miki karya ne ,? Toh idan kin ce karya ne ɗaga rigar ki aga kirjin ki , nace ɗaga rigar ki mu ga kirjin ki ƴar iska jaririyar ƴar bariki ,' Toh kai kachalla ai sai ka cire rigar mu ga kirjin naka domin cire zargi cewar madam saly," sunkuyar da kai falmata tayi tana matsar ƙwalla Koh kafin su farga ɗan liti yayi charaf ya kaiwa gaban rigar falmata chafka , baiyi wani jinkiri ba ya sa karfin tuwo ya balla baturan da suke jere gaban rigar , yana cewa Dan uwar ki rigar uban waye ya saya miki ba ni ba ?? Yau sai mun ga karshen karya ," Da gudu yakaka ta karaso wurin ganin ana neman tozarta ƙanwar ta ayi mata tsirara cikin taron maza da mata ," Ƙoƙarin raba hannun ɗan liti da jikin rigar falmatan ta fara , tana cewa Ɗan liti ka sake mata riga meye hakan ? Wai ina ruwan ka da harkar mu ," Wata dariya ɗan liti ya sake , kin ji koh madam saly nace kin ji koh ? Da bakin ta take ambaton ta a jinsin mata , shegu munafukai , yau me raba ni da ku sai Allah tun da kuka jawo min asara , yana gama faɗin hakan ya ingije yakaka tayi faɗuwar ƴan bori , kafin ta taso , ya sanya dukkanin karfin sa ya jijjiga falmata gami da keta mata riga , ya sanya hannayen sa duk biyu ya cisge tsunman da take ɗaure kirjin da shi ,ya murɗa hannayen ta tare da lanƙwasa su baya ya banƙaro kirjin ta gaba wanda hakan ya bayyana haliltar kirjin ta tsai a tsaye ," Wani irin guntun salatin da ba'a ƙarasa shi ba tare da shewa da ihu sune suka cika wajen daga bakunan mata da mazan da ke wajen , cewa suke wallahi chika ce , laaah , A toh idan har yanzu ba'a yadda ba sai na ɗaga muku ƙasan shi ma ku gani dan gaba kar a karkace a kuma sharo wata ƙaryar ace mata-maza ce gara a ga ƙarƙashin , Nan dai wasu suka fara ihu suna cewa a ɗaga su gani a ɗaga su gani Da gudu yakaka ta taso tare da yi wa falmata rumfa da jikin ta idanun ta kuwa tuni suka fara zubar ruwa , cewa take menene hakan ?dan Allah kuyi hakuri ku kƴale ta , ƙanwata miskiniya ce makauniya ce , ni ce da laifi , ni nace ta koma shigar maza , kowanne hukunci zaku yi mata ku min a madadin ta ,' tana faɗin hakan tana warware ɗankwalin kan ta tare da rufawa falmatan da take risgar kuka , cikin tsokar jikin ta take jin idanun jama'ar da suke zagaye da wajen , cikin ran ta tana jin wani irin rauni da bata taɓa jin irin sa ba tabbas an cuce ta an tazorta ta matuƙa an tsaraita ta a gaban jama'a Yagana ma matsar ƙwallar tausayin falmata take , Madam saly kuwa wani malalacin kallo take bin su da shi ," Yanzu daman dan uwar ki yaks ƙarya kuke min ? Toh kuwa yau yau ɗin nan zaku bar min gida ƴan iska maƙaryata , da sauri yakaka ta matso gaban saly ta shiga rokon ta akan ta taimaka kar ta kore su domin basu da kowa ," Da ƙyar da jibin goshi larki da hema suka sanya baki wurin taya yakaka bawa madam saly hakuri saboda tausayin yaran da ya tsirga musu , bayan sun ƙora ɗan liti wanda ya zama ziga-zigi yana sake tunzura madam saly ta kori su yakaka , ya dage akan cewa turo su C.I.D aka yi wanda hakan ke ruda madam saly , sanin cewa ita ba mutum bace mai gaskiya , sanna a cewar ta kewaye take da makiya ƴan hassadar ta . Ficewa yayi bayan ya tabbatarwa yakaka duk inda kuɗi suke ta nemo ta biya sa kayayyakin da ya sissiyawa falmata domin shi bai yin asara koh ta sisin kobo , kuma kar falmata ta sake taka ko da kofar ɗakin sa ne , idan har kuwa ya gan ta a gaban ɗakin sa babu abun da zai hana ya kirɓe ta ,' Toh yanzu da ku ka nace kar a kore su akan ku zasu dunga kwana su biyun ? Kun san dai ku ukun ma a matse kuke tamkar kifin gongoni , cear madam saly Da sauri yakaka wacce har lokacin rungume take da falmata da take ta faman sauke ajiyar zuci akan kukan da ta sha , tace Ni zan dunga kwana a kan benci cikin rumfa idan ya so falmata ta kwanta tare da su a ɗakin idan kin yadda , Sai da madam saly ta wurga mata harara domin har yanzu tana ɗan jin haushin su Ƙya ce haka mana dan kun samu na ƙyale ku algungumai , ni dai ku kiyaye ni kar ku bari na sake kama ku da wani laifi domin gaba ko kun fi kuturu naci sai kun bar gidan nan , tun da kin zaɓi kwanan kan benci a cikin shagon toh ke kika sani sautun mahaukaciya , duk abun da ya biyo baya ki kuka da kan ki , kar ki ce ban faɗa miki ba , Ba tare da fargabar kome ba yakaka ta amince da zantukan madam saly cikin ran ta tana sa mata albarka , Wanene Alhaji basko ?? Aina kika san shi ? meye haɗin ki da shi ? Kuma ta yaya yasan cewa ke mace ce ?? Su ne tambayoyin da yakaka ta jerowa falmata lokacin da take taya ta shiryawa cikin ɗaya daga cikin kayan da take warewa take ajiyewa falmatan su , Ba tare da jinkirin kome ba falmata ta fayyace mata kome , Hawaye ne yake sauka bisa kumatun ta , meyasa mutanen duniya suke son zukatan su ?meyasa taimako domin Allah yayi ƙaranci meyasa zalunci ya yawaita , meyasa fasikanci ya zama mahaɗin rayuwar mafi yawan mutane ,??? Meyasa meyasa ? Ji tayi tsanar dukkanin mutanen da suke kewaye da duniyar ta ya kama ta idan aka ɗauke ƙanwar ta ,' Nan gaba kar ki sake yadda da kowa falmata , idan na ce kowa ina nufin kowa ,! Kin ji ko ? Ba tare da falmata ta hakiƙance da inda kalaman yakaka suka dosa ba ta amsa mata da toh ," Daga ranar yakaka ta koma kwanan cikin rumfar da suke sana'ar su ciki , yayin da idan kafafu sun yanke a wurin kamar sha biyun dare sun riga sun gama sana'ar su, zuwa lokacin duk ƴan iskan sun watse wasu sun shige ɗakunan su tare da abokan iskancin su sai ta haɗa teburan da suke gaban kujerun , guda huɗu ta shimfiɗa zanin ta akai tayi matashi da hannunwan ta tare da rufuwa da wani zanin , sai tayi baccin ta ba tare da tsoron duhu da shirun da wajen yayi ba ko kuma tsoron ƴan iskan da ka iya kawo mata farmaƙi , wurin kwanan ta na cikin ɗakin kuwa ta barwa falmata , A haka kwanaki suka fara miƙawa har yau da ake kwana na uku da faruwar lamarin falmata ta gagara sakewa dan kuwa tuƙuru ƴan matan gidan suke tsokanar ta , har suna cisge mata ɗan kwali , suna faɗin ta koma shigar maza ta fi yi mata kyau , da hakan ba ƙaramin sanya ta takaici yake ba , sai dai tayi matuƙar koƙari wajen boye damuwar ta domin kar ta jefa yakaka cikin damuwa ita ma , duk wani abun da idon ƴakakar bai gani ba game da tozarcin da ake yi mata bata faɗa mata . Juyi yake ta yi akan katifar sa kaɗan-kaɗan yana jin wani sabon yanayi da ya fara ziyartar sa a tun lokacin da agogon wayar sa ya nuna masa sha biyun dare cib wanda a lokacin yana kan computer sa yana wani aiki sai dai wannan yanayi da ya fara ji yana taso masa ya sa shi rufe computer tare da wani irin bingirewa akan katifar sa tamkar dai an tunkuɗa shi ,' daran ranar ya zo dai-dai da cikar sa shekaru talatin cif a lissafin watanni turawa , Miƙewa yake so yayi ya fita ya ɗauro alwala , domin ya samu damar raya ƙarshen daren da ibada Kamar yadda yake aikata hakan jifa-jifa , sai dai ga mamakin sa ya kasa tashi , haka yake jin sa kamar an ɗaure shi ko kuma an aza masa wani abu mai nawi an danne shi , yana jin sa a wani yanayi mai cike da fargaba da tsoro zuciyar sa na wani irin bugu , yana jin sa ɗan mitsitsi kuma sakayau tamkar ba shi ba , shi ya san ba bacci yake ba ba kuma a farke yake ba sannan ba mafarki yake yi ba , yana jin sa kawai a wata duniya ta daban , duk yadda ya so yayi addu'a ya kasa , Haka ya shafe tsawon awannin karshen daren har zuwa lokacin da alarm ɗin da ya saita a wayar sa ya fara rangwaɗo sautin kiran sallah cikin zazzaƙar muryar balarabe , wanda cikin ikon Allah ya ji cimak wannan nawin da yake ji ya hana shi motsi , babu shi tamkar dai an sauka a kan sa , da gudu ya miƙe tsaye , jikin sa ya jiƙe sharaf da gumi , wannan tsoron da yake ji ya kau , sai dai har yanzu ɗan sauyin da yake ji a jikin sa yana nan , amma cikin ran sa sai ya dangan ta hakan da zamantowar sa cikakken ɗa namiji lafiyayye da ya kai minzalin da ya kamata ya buƙaci mace , duk da cewa shi youssouf ba manemin mata bane , bai taɓa zina ba , bai taɓa kusantar kowacce mace ba duk yadda ya kai ga cuɗanya da matan bariki matan banza , shi mutum ne mai tsantsani ta wannan fannin , Da sauri ya ɓude ruwan leda ya juye cikin ɗan bokatin da yake yin amfani da shi wurin yin wanka , ya cika shi taf da ruwa gami da sunkuta ya fito daga tantin sa zuwa ɗan bayan gidan da aka samar masa na wucin gadi wanda yake mallakin sa shi ɗaya ,' Ruwan na da sanyi sosai dan haka yayi tunanin zai taimaka wurin kawar masa da yanayin da yake ji a jikin sa , sai dai ga mamakin sa daga lokacin da ruwan ya sauka akan fatar jikin sa , ya ji tamkar an ƙara masa masifa ne domin gaba ɗaya tsikar jikin sa tashi tayi da ya sa dukkanin wasu jijiyoyi na jikin sai da suka taurara tare da fitowa baro-baro ,wani irin ƙullewa ya ji marar sa tayi , Ba shiri ya sanya tufafin sa gami da ɗauro alwala ya dawo cikin tantin sa , a daddafe ya idar da sallah saboda yadda marar sa take tamkewa tana sakewa , Kwanciya rub da ciki yayi bayan ya sanya ɗaya hannun sa ya riƙe marar sa ,tun da yake bai taɓa tsintar kansa cikin wani hali makamancin wannan ba, a hankali ya fara jin ciwon marar yana raguwa , wani ɗan daddaɗan bacci yana fisgar sa a sakamakon lafawa da ciwon yayi tare da daɗin ƴar sassayan iskar asuba da take shigowa ta tsakankanin rumfar tantin sa ,,' Bacci yake yi sosai da bai samu irin sa ba duk tsawon daren jiya , kafin sautin kiran wayar sa ya tashe shi , miƙa hannu yayi ya jawo wayar tare da miƙewa zaune saboda sautin kiran ya bayyana masa girma tare da muhimmancin mai kiran na sa Allô mama oui meilleur sava,? Daga chan ta amsa masa sava bien yaro na ya kwanan ka ? Da dama kou ? Ɗan jim yayi yana son faɗa mata yadda yake jin jikin sa saboda ya saba bayyana mata duk wata damuwar sa , sai dai kuma yanayin da yake jin yayi masa nawin faɗi a kan harshe musamman ma ga mahaifiyar sa * Daga bangaren ta kuwa zuciyar ta ce ta buga a sakamakon tunowa da mummunan mafarkin da tayi akan sa asubahin daren jiya da ya haddasa mata rashin nutsuwa , da ya sa tun asubah take neman layukan sa domin ta ji lafiyar sa kou ta samu kwanciyar rai amma rashin kyaun hanyoyin sadarwa ya sa sai yanzu da safe ta cimma nasarar samun sa a wayar ," Yaro na yi min magana mana hankalina ya tashi , Da sauri ya katse ta ," da dama umma ya ɗaura da tambayar ta ina merama ? Ta amsa masa da lafiya take , " Cigaba tayi da tambayar sa lamuran da suke gudana daga wurin sa , yana bata cikakkun amsoshin da suka gaza wurin gamsar da ita , zuciyar ta ta gaza nutsuwa duk lokacin da ta tuno da mafarkin da tayi sai ta ji bata son ta daina jin sa a waya , inda da hali so take ya kasance a idanun ta cikin waɗannan kwanakin dan tana jin kamar wani abu marar daɗi zai faru da su, duk da ta san sau dayawa mafarki bai zama gaskiya a mafi yawan lokuta daga shaiɗan yake , kuma ita bata da ikon kare kan ta ma bare wanin ta , ta san ko da agaban idanun ta yake , bata isa ta bashi kariya ba , illah addu'ar ta da ka iya yin tasiri akan ko ma menene , kuma duk nisan tazarar da ke tsakanin su ta san addu'ar zata isar masa , sanin da tayi youssouf ba sosai sosai yake tsayuwa yayi addu'a ba , shi dai mai tsayar da ibadun sa na farillah ne , bayan su sauran lokutan sa ƙorafi yake aiki ya cinye su ,wanda ita kuma hakan bai mata daɗi , ta san duk wata nasar da kariya daga wurin ubangiji ake samun su , dan haka a yanzu ma sai ta sake tunasasshe sa game da girman addu'a inda shi kuma ya tabbatar mata da yana yi ,' Sallama yake shirin yi mata , sai kalaman ta suka katse shi ,"Tu es notre lumière, notre joie, et pour toi nous donnerons le meilleur. En te souhaitant une vie abondante et en bonne santé.Joyeux anniversaire mon fils!,' Allah shi yi maka Albarka shi kare ka du inda kake yaro na , Murmushi ne ya suɓce masa halin da ya wayi gari cikin sa ya sa ya ma mance da yau take ranar zagayowar haihuwar sa kalaman ta na yanxu suka suka tunassashe sa,'amsa ya maida mata cikin tsantsar ƙaunar ta da yake ji cikin ran sa ," merci mama je t'aime," Daga bangaren ta ajiyar zuciya ta sauke bayan kammala wayar su , babu laifi ta ɗan samu nutsuwar zuciya , sai dai ta kuɗurce a ran ta zata ƙara ƙaimi wurin neman kariyar ubangiji akan ta da ƴaƴan ta , daga makiyan su da ta san suna kewaye da su , Juyowar da zata yi domin nufin ta shiga ɗaki ta fara sallar walha , idanun ta suka sauka akan hajiya uwa wacce take yi mata wani irin hargitsattsen murmushin da baza ta iya hasashen nufin sa ba , bata san lokacin da ta wanzu a wurin ba domin baya ta bawa kofar shigowa falon nata na ciki , Tsawon zaman su baza ta iya tuna rana ta karshe da hajiya saratu ta tako kafafun ta sashin ta ba , basa shiga sassan juna iyakacin su , su haɗu a bangaren mai martaba idan haɗuwar ta kama dole , ko kuwa wurin gaishe da hajiya uwa ,' Sannan tayi mamakin ganin ta ita ɗaya kai tsaye har cikin bigiren ta da sai an nemi iznin ta kafin a shigo ,' a sanin ta tare da tawagar ta hajiya saratun zata iso kuma karƙashin jagorancin shugabar bayi ta bangaren ta ,' Da kallo ta bita lokacin da take yi wa kan ta mazauni akan shimfiɗar alfarma da ta tashi daga kan ta yanzu ,' Hala uwargidan mai martaba sarauniya tayi mamakin wanzuwa ta gaba gare ta a yau ,? Shi yassa aka gaza wurin taryaa ta kamar yadda ya kamaace ni , Fuskar ta babu walwala ta ce ," Ban yi mamakin zouwar ki nan ba saratu , shin ƙaƙa za'ai mamakin wanzuwar macce a kowanne bangare cikin gidan amren ta ? Sannun ki da isowa ina miki lale marhaban ,' zama tayi daga ɗaya bangaren shimfiɗar ,' Suka yi kallon kallo na tsakiyar ido , kafin saratu ta ce ,' Yau yariman maraɗi ke cikkace shekarun sa talatin cikkin duniya , kou ba hakka ba ? Kallon mamaki hajiya safiyya ta bi ta da shi tana jin bugun zuciyar ta na ƙaruwa a hankali mafarkin ta na jiya ke dawo mata da fuskar saratu da ta gani cikin mafarkin ," janye idanun ta tayi daga kan ta ," Ƙaƙa kin ka sani ? Kafin ta rufe baki saratu ta amsa mata cikin wani yanayi mai tattare da ma'anoni ,ƙaƙa uwa zata kasa sanin ranar haihuwan ɗiyan ta ,? ??? Guntun murmushin fatar bakin ta safiyya tayi ,'haka ne kin yi gaskiya ,! Kiraye ma ni shi na taya shi murna shine abu da ya kawo ni gaba gare ki ," Tsam hajiya safiyya tayi tun haihuwar youssouf yau shekaru talatin saratu bata taɓa taya shi murnar zagowar ranar haihuwar sa ba sai yau ,? Sama ta ka zata ce zata taya shi murna ? Wallah banza bata kai zomo kasuwa ,! Ta bangaren biyamuradi youssouf kuwa tun yana cikin yin waya da umma yake jin kira yana shigowa wayar , Yana gama magana da umma ya bi bayan kiran da ya gani daga wata bakuwar lamba daga ƙasar su , sai dai har kiran ya tsinke ba'a ɗaga ba , yana shirin ajiye wayar ɗan guntun sako daga lambar ya shigo wayar sa ," Mon frère, je t'aime tellement. Que toutes les meilleures bénédictions te parviennent aujourd'hui et pour toujours. !Bon anniversaire.! Sakon taya murnar zagayowar haihuwa ne ,duba lambar ya sake yi yaga bai san ta ba dan haka kawai sai ya share , ya fara koƙarin kiran layin maimouna kamar yadda suka saba kullum safe Neman iznin shigowa aka yi ya bada izni aka shigo , abincin karyawar sa ne , aka shigo masa da shi, Da hannu yayi nuni da a ajiye masa abincin , Allo ma jolie fille Allô joyeux anniversaire mon amour , Ɗan jim yayi yana tunanin ta yaya maimouna ta san yau ranar zagayowar haihuwar sa ,? Shi dai ba shi ya sanar da ita ba , ' Princesse wa ya fadi miki wagga batou ? Cikin dariya ta bashi amsa a iska ta ji , murmushi yayi tare da share batun , suka cigaba da hirar su cikin nutsuwa tare da ƙaunar junan su , Wayar su ba mai yankewa da wuri ba ce ,musamman yau da daɗin soyayar ya juyo , dan haka riƙe da wayar ya fita ya wanko bakin sa ya dawo ya zauna cin abincin sa , Tashin farko ya kai abincin bakin sa ba tare da bismillah ba , saboda hirar maimouna ta ɗauke hankalin sa , haka har ya cinye abincin tas tana zuba masa zantukan soyayya , sai dai me ? yana gama ci ya ji marar sa ta murɗa , ba shiri suka yi sallama ,' ga mamakin sa sai kuma ya nemi ciwon ya rasa , Dan haka ya tashi yayi shirin sa tsaf cikin kayan sa na soji , ya fito Ya tarar da duk sauran da ke ƙarƙashin sa ma sun shirya domin a yau zasu ɗan yawata ne cikin daji ta sama ta hanyar jirgi mai saukar ungulu,'helicopter"domin su ga wuraren da ƴan tawayen boko haram suke da mafaka su tabbatar basu tsallaka iyaka sun shiga yankin ƙasar su ba ,' Suka hau jirgi ya ɗaga da su , sun ga wuraren da boko haram suka yi bigire na dindin-din cikin dazuzzuka tare da matan su da ƴaƴa suna rayuwar su cikin walwala tare da jin daɗi fiye ma da al'ummar cikin gari , abun da ya ɗaure kan youssouf kenan , ƙaƙa ƴan ta'adda irin wannan suka samu bigire cikin ƙasa kamar nigeria ? Shin wake ciyar da su ? Wake kai musu makamai ? Waye ke da alhakin basu magunguna zuwa kaƴan bukatun yau da kullum ?? Tabbas akwai lauje cikin naɗi ,' Sun samu kimanin awa guda a sama suna shawagi kafin suka sauko , kai tsaye ya wuce cikin tantin sa ya kwanta , gaba ɗaya yau ya gaza gane kan sa wani iri yake jin sa tamkar akwai wanda ke sarrafa shi a gefe , yana ji kamar su biyu suke gudanar da kome , amma kuma shi baya ganin kowa ," Haka ya yini babu walwala , sun yi waya sau biyu da umma wacce take sake jaddada masa ya riƙe addu"a tare da yawaita karatun kur'ani sai dai kuma abun da bata sani ba shine yau sam-sam ya gaza yin addu'a a yanzu haka da yake kwance ya gagara tashi yayi sallar azahar alhalin kuma la'asar har ta gota , karfe huɗu ma ta wuce , sannu sannu ya fara jin wannan yanayin da yake ji na safe yana sake tado masa , " wata irin mahaukaciyar sha'awa yake ji kamar zai fidda wani sashi na jikin sa ya ajiye koh ya huta ," shi kuwa yau wacce irin masifa ce ta same shi ? Ita ce tambayar da yake yiwa kan sa ," Sau biyu sojojin da ke da alhakin kula da lafiyar sa suna leƙowa su duba shi domin sun ji shirun yayi yawa , koh ɗan masallacin da suka tayar suke jam'i cikin sa bai zo yayi sallah tare da su ba a yau baki ɗaya , Ga mamakin su duk shigar su a zaune suke tadda shi , sannan kuma yana tabbatar musu da lafiyar sa lau babu abun da ke damun sa , dan haka sai suka kƴale shi , Zuwa magariba youssouf ya fara gagara iya riƙe kan sa domin tashin hankalin da yake jin kan sa a ciki ya wuce tunanin sa ya wuce yadda yake ji idan bai sha burkutu ba , wannan karon ji yake yana gab da mutuwa idan bai samu biyan bukatar sa ba , Ina zai samu mace a yanzu alhalin yana cikin jeji ? Yaya zai yi ? Dama a cikin gari yake sai ya fita ko'ina ne ya samo wacce zata taya shi ya kauda bala'in da yake ji ,' miƙewa yayi a dudduƙe ya ɗauki walet ɗin sa tare da ID card ɗin sa , har yayi nufin fita sai kuma ya fasa lokacin da ya kalli jikin sa ya ga yadda ya ke , wani kunya da takaici suka dirar masa , lokaci guda wani duhu ya mamaye masa kwakwalwa da ya sa nan take ya mance da wani batun kunya illah umarni da yaji ana bashi akan ya tafi , Yana daga cikin ɗakin ya danna kiran masu kula da shi ta wayar hannun sa , ba tare da jinkiri ba suka zo , yace su kawo masa mukullin mota zak ɗan fita , " jim suka yi ,toh sai dai basu da ikon musa umarnin sa dan haka suka kawo masa mukullin motar suna jiran su ji yayi musu umarnin su mishi rakiya wani wurin , sai suka ji ya sallame su , ficewa suka yi suka bar shi ," suka nufi bakin masallaci domin yin shirin sallar isha'i Suna tafiya shima ya fito ya buɗe motar ya faɗa ,' ya jaa ta da mugun gudu , ya hau titi tare da nufar cikin garin maiduguri a wannan daren ,' Gudun da yake ba na hankali bane , bai ko tsoron dare da yadda garin yake haɗe da hadari sai walƙiya ake yi, bai tsagaita ba sai da ya shigo da'irar birnin maiduguri lokacin sha ɗaya da rabi na ɗare har ta gota, cikin garin babu kowa kan titi sai sojoji ƴan uwan sa da suna hango motar ta sa mai ɗauke da fentin launin kakin soja suke buɗe hanyoyin da suka bi suka tottoshe saboda tsaro, shawagi ya fara yi da motar marar sa na cigaba da karta masa har yana ganin duhu-duhu , ya haɗa zufa sai tsuma yake yi, ina zashi ? Shi ba wani sanin kan garin yayi ba guri ɗaya zuwa biyu ya sani , daga barikin garin wurin abokin sa , sai kuma wurin sayar da burkutu , karya kan motar yayi ya lokacin da ya ji kamar an umarce shi da ya tafi zuwa wurin sayar da burkutun , a chan zai samu wacce zata iya kula da shi , Yana yin fakin ɗin motar ya fito ba tare da ya damu ya rufe murfin ba ya fara taku yana bin hanyar da zai sada shi da cikin gidan hannun sa ɗaya ya riƙe marar sa , da layii ya ƙaraso cikin rumfar , sai dai bakikkirin ya tadda wurin , babu kowa an watse kujerun gurin kansu a tattare suke, wani irin jiri ya ji yana kwasar sa , ya tabbata yau mutuwa zai yi , Tun shigowar sa yakaka wacce bata daɗe da kwanciya ba, bayan ta tattara cikin shagon ta kintsa kome, sai dai ta gagara bacci saboda tsinkewar da zuciyar ta ke yi wanda ta danganta hakan da tsoron tsawa da walkiyar da ake yi , Taji shigowar sa a tun takun sa na farko a cikin shagon , tsumu tayi cikin zanin rufuwar ta , tana sake jin bugun zuciyar ta na ƙaruwa da duk wani motsi da yake ,wanene cikin daren nan ? Koh wani ne yayi mantuwa ? kaƙƙarfan kamshin turaren sa shi ya ziyarci hancin ta , kamshin da ya ɗauki tsawon kwanaki a hancin ta kafin ta daina jin sa a wancen haɗuwar ta su ,' Kamshin na musamman ne dan haka sai ta zame abun rufuwar daga kan ta dan ta samu damar shaƙar ƙamshin da kyau cikin ran ta kuma tana ƙwaɗayin ganin fuskar sa , Da ɗan tazara a tsakanin su domin shi yana tsaye daga bakin kofar ta ciki yana fuskantar inda yakaka ke kwance sai dai bai kai ga fahimtar mutum ba ce saboda babu wadatar haske kuma baki ɗaya bai cikin hayyacin sa , Sosai ta buɗe fuskar ta tana ƙare masa kallo ta cikin ɗan hasken da yake shigowa ɗakin da taimakon hasken hadarin da ya gangamo cikin duhun daren , bata gani ainahin kamannin fuskar sa sai dai siffar jikin sa da take gani , gani tayi ya sunkuya yana riƙe da cikin sa Tsawa aka yi tare da walƙiya da ya haddasa yakaka tsorata har ta miƙe zaune , motsin ta ya sanya shi ɗago kan sa ,walƙiyar da aka sake yi ta hasko masa farar fuskar ta ta zuba masa ido tana kallon sa daga inda take zaune ,' Wani tsallen farin ciki zuciyar sa tayi, da sassarfa ya fara takawa yana nufar ta tamkar mayunwacin zakin da ya kwan uku ba abinci , Baya ta fara yi akan bencin tana matsawa , cikin in'ina tace ,' Babu ruwa ya ƙare ,mun ruga mun tashi an gama aiki sai gobe da rana ,' Kalaman ta sun zo dai-dai da ƙarasowar sa gaban ta , baiyi wata wata ba ya miƙa hannu ya ɗago ta daga kan bencin ta hanyar ɗago kafaɗun ta ya tsaida ta akan kafafun ta , ba kuma tare da ya ce da ita ƙala ba ya juya tare da jaan hannun ta da ya riƙe nufin sa ta biyo shi ,' Waiwayowa yayi jin ta turje tana ƙokarin zame hannun ta da ya riƙe tamau , Cikin wata irin dusasshiyar murya da take fitowa daga ƙarƙashin maƙoshin sa yace ," Ki taimaka min kar na mutu ko nawa ne zan biya ki ki taimake ni ," Daga haka ya juya yana jaan hannun ta , bata yi turjiya ba ta fara bin sa kafafun ta ko takalma babu ," kalmar taimako da ya ambata tare da wani abu da take ji yana fisgar ta a game da shi ya sa ta bi shi ,' Sun zo tsakiyar filin gidan aka fara yayyafi ,' yakaka ta sake tsayawa saboda gargaɗin da zuciyar ta ke yi mata akan yunƙurin bin mutumin da bata sani ba cikin dare zuwa wurin da bata kai ga sani ba wai shin ina hankalin ta yake ne ?? Juyowa yayi aka saki tsawa da walkiya tare da ƙaruwar ƙarfin ruwan sama , haɗa ido suka yi ta hasken walkiyar suka kalli juna na wasu dakikai ba tare da kowannen su ya samu damar magana ba ," Cikin idanun sa ta hango ruɗanin da yake ciki , tare da wani abu da ya taɓa zuciyar ta da bata kai ga fahimtar yanayin sa ba , sai dai koma menene yayi tasiri matuƙa wurin raunana mata zuciya ta yadda ta ji kowanne irin taimako ne zata iya yi masa , zata mishi kome yake so , tana nufin kome , A bangaren biyamuradi youssouf kuwa shi ma kallon cikin idanun ta ya taɓa shi , ya hango rauni tare da zallar ƙuruciyar da ke tattare da ita ,sai dai sun gaza tasiri agare shi domin daga lokacin da ya riƙo hannun ta ya fara jin wani irin nutsuwa tare da ɗaukewar ciwon da yake ji ,har da wani danshi danshi yake ji a ƙasan ran sa wanda ya tabbatar masa ita zata iya fidda shi halin da ya ɗauki tsawo awanni ashirin da huɗu cikin sa , yana jin zai iya biyan ta ko nawa ne domin ta yadda da shi , Ganin bata ce kome ba ya sa shi ya cigaba da tafiya riƙe da hannun ta sai dai wannan karon tare suke jefa kafafun su a jere tamkar sabbin masoya cikin samun amincewar yakaka da ta hakiƙance zata taimaka masa , " Bai saki hannun ta ba sai da ya dangana ta da cikin motar sa ba tare da fargaban kome ba yakaka ta shiga ta zauna tana shaƙar ƙamshin turaren sa da ke da matuƙar tasiri agare ta ," Da ƙarfi ya fisga motar wanda yayi dai-dai da fara saukar ruwan sama da matuƙar ƙarfi , wani ƙaramin Guest house ya nufa wanda yake ganin sa akan hanyar shigowa gari , cikin su babu wanda yake ce da ɗan uwan sa ƙala ba har suka isa , bai wani sha wahala ba wurinnsamar musu da ɗaki zamantowar sa jami'in tsaro , Riƙe da hannun yakaka wacce ta zamto tamkar rakumi da akala ya danna kai cikin ɗakin ,' Daga lokacin da suka sanya ƙafa cikin ɗakin kome ya fara kasancewa nan ne mafarin hargitsin rayuwar su , sun gudanar da kome cikin amincewa tare da tallafin junan su , yakaka bata hana biyamuradi kan ta ba wanda ita da kan ta baza ta iya faɗin dalilin ta na sadauƙar masa da mutuncin ta ba ita dai ta san koma wanene wannan mutumin da ya kasance mutum na farko da ya fara kasancewa da ita a wani bigire kuma cikin wani yanayi irin wannan ,akwai wani al'amari mai girma a tare da shi .' A bangaren biyamuradi kuwa tsintar kan sa yayi a wata duniya mai nisa wacce take tare da wani irin daɗi da sanya nishaɗi da bai taɓa jin makamancin sa ba , ji yayi ko da dakika guda baya fatan wani abu ya gifta da zai katse masa jin daɗin sa , Yana jin zai iya mallakawa yarinyar nan kome ta buƙata , idan ya ce kome yana nufin kome ." Ta hasken ranar da ya hasko ɗakin ta tsakanin ɗan yalolon labuƙen ɗakin yakaka take ƙarewa fuskar biyamuradi kallo , komen sa mai kyau ne babu abun da ya fi ɗaukar hankalin yakaka irin jajayen laɓɓan sa ," tambayar kan ta take daman maza ma na shafa jambaki ? hannu take niyyar kaiwa fuskar sa ta ga ya buɗe idanun sa a firgice kamar ba wanda ke bacci ba ," Da sauri ta jaa baƴa tare da maƙurewa a jikin gadon ," Zama yayi yana me ƙarewa ɗakin kallo kafin ya waiwayo kan yakaka tare da wani irin kallo da ta kasa tantance ma'anar sa ya watso mata tambayar da ta shayar da ita mamaki ," Wacece ke ?????? Assalamu alaikum masoya, ku min afuwa da jinkirin da aka samu kafin zuwan wannan shafin , da kuma rashin baku amsoshi n sharhn ku a shafin baya duk hakan ya faru ne sakamakon aiyuka da suka sha kaina , ina fatan na wanke kaina da wannan mafi tsawon shafi da na rubuto muku ?? Idan haka ne nima kar ku min rowar sharhin ku ,' ku faɗi ra'ayoyin ku,akan wannan tafiya tamu, a wannan karon zan bada lokaci mu tattuna tare domin ƙarin armashi , na gaishe ku kyauta !!! [6/24, 10:59 AM] +234 701 013 7848: MAFARI Hargitsin Rayuwa Umm"muaz 19 Wacece ke ?? Ni ni nice yakaka ," Ya ka ka ? Ya maimata sunan kamar me koyon magana ,' Ina ne nan ? Waye ya kawo ni nan ? Me muke yi anan ?? Wannan karon a tsorace yakaka take kallon sa ,"kar dai mahaukaci na biyo ni yakaka na shiga uku ," ? Tsawar shi ita ta katse mata tunani cikin hargagin su irin na soji yake sake maimaita mata tambayoyin ," Fashewa tayi da kuka cikin rikici ta fara cewa ," ni ka mayar da ni gida nima ban san ina ka kawo ni ba ,! Tare da tarin wani al'amari da ya shallake tunanin sa ,' ya maimata tambayar ,'    Na kawo ki ? Eh ba kai bane jiya ka ɗauko ni cikin dare ka ce zan taimaka maka shine ka kawo ni nan ," Kamar a majigi ya ji al'amuran da suka faru gare shi tsawon yinin jiya sun fara komawa baya suna giftawa ta cikin ƙwaƙwalwar sa tare da hotuna ," har zuwa kan al'amuran da suka gudana tsakanin sa da yarinyar da take gaban sa a yanzu ,"   Wani irin sufa yayi ya wawuro yakaka wacce ta cika tayi fam ta tsattsare shi da ido ,"     Riƙe ta yayi gam ,! Yarinya yi gaogawa sanar da ni mafalki muke faɗa mini ba gaske bane ni nayi tarayyah da ɗiyar mutane ta hanyar banza , ki ce mafalki ne, ya ƙarasa zancen yana jijjiga ta .     Gaba ɗaya ya shiga ruɗani ji yake tamkar ya haukace yana son ya gano wace masifa ce ta kunno cikin rayuwar sa daga jiya bayan wacce yake ciki na shan burkutu? Shi bai sha'awar zina hasalima yana ƙyamatar masu yin ta ," wani tsoro ne ya ziyarce shi da ya sa shi angaje yakaka lokacin da ya tuno da girman laifin sa wurin ubangiji ," zuwa yanzu ya gama tuno da kome da ya faru da shi  ," Bai san lokacin da ya fashe da kuka ba da dukkanin karfin sa , kuka yake babu kakkautawa ,"ji yake kamar ƙasa ta tsage ya shige cikin ta ," zuciyar sa ke sake raɗa masa ya tabbata mutumin banza gafalalle lalatatce , " Cikin mamaki tare da shakkun samuwar cikakken hankali a gare shi yakaka ta ware ido tana kallon sa tare da nutsuwa cikin shirin ko ta kwana idan ya kawo mata chafka ta daka tsalle zuwa waje ," Sai da yayi kukan sa mashi'i cikin ransa kuwa ya rasa takamaimai addu'ar neman tuba da zai yi kowacce ya kamo sai ya ji ta tayi ƙanƙanta wurin rokon Allah akan yafiyar zunubin da ya aikata ," chak ya tsaya da kukan lokacin da ya tuno da dauɗar da ke tare da shi ," A sukwane ya nufi kofar da bai da tantama ta banɗaki ce ,"ba tare da ya kuma kai duban sa ga yakaka ba wacce take ɗosane a gefen gadon tana ƙare masa kallo ," Maimaita wankan tsarki yake yana kuka , sai da ya gaji dan kan sa ya sanya tufafin sa gami da fitowa ," Karaf suka haɗa ido da yakaka wacce ta zubawa kofar banɗakin ido tamkar mai tsumayin fitowar sa ," Kallon ta yayi na ƴan wasu dakikai da idanun sa da suka yi jawur ," cikin ran sa yana gorantawa kan sa yanzu wannan ƴar ficiciyar yarinyar da bata wuce merama ba ita ya saukewa larurar sa ,'? Shin wai ma meya sa ita yarinyar nan bata yi masa turjiya ba yana tune da shine mutum na farko da ya fara tarayyah da ita , shin ko ita ma abun da ya faru da shi ne a jiyan ita ma ya faru da ita ? Toh amma kuma ai ita ta so taƙi yadda da shi sai dai a ƙurarren lokaci ne , har yanzu yana tuno amsa kuwwar kalmomin ta waɗanda suka gaza tasiri wurin daƙile shi ga aikata abun da yayi niyya a jiya da yanzu kuma kalmomin suka zama tamkar ɗigar ruwan dalma a kunnuwan sa , bai ko son tuno da su ," ko ma menene ita ma tana da nata laifin a wurin shi na yadda ta gaza yin hoɓɓasa wurin dakile fadawar su ga halaka ," Tsaki ya ja tare da auna mata harara , ki tashi na maida ki inda na ɗauko ki ,! Tafiyar kuramen suka sake yi babu um ba a ah ," kowannen su yana sauraren taɗin zuciyar sa , Ga yakaka ita har yanzu bata daina mamakin mutumin da bata kai ga sanin ko da sunan sa ba har zuwa yanzu , bata wani jin nadama koh damuwa akan halin da suka kasance ciki tare idan aka ɗauke ɗan raɗaɗin da take ji a jikin ta, dalili shine bata kai ga sanin girma tare da darajar budurcin ta ba , rayuwar kaɗaici suka taso a ciki , ko a garin su a ware suke cikin jama'ar gari sannan mahaifiyar su bata yi wani yunƙuri wajen nuna musu girman budurcin su ba , basa makaranta illa mahaifin su da yake koyar da su karatun sallah a gida ," Chan wani saƙo na zuciyar ta kuwa yaba gayu tare da gogewar biyamuradi yousouf take har ma take jin yana matuƙar burge ta , hakan ya sa take yawan satar kallon sa zuciyar ta na tuno mata da mahaukaciyar soyayyar sa da ya gwada mata a daren jiyan tamkar zai cinye ta ,' Ga biyamuradi youssouf kuwa tunane-tunane barkatai cikin kan sa har ya rasa takamaimai na kamawa , shin yaya iyayen sa zasu ji lokacin da labari ya isar musu na irin lalacewar da yake ace wai bayan shan barasa shi youssouf har neman mata ya fara yi yayi nadama da bai amince an ɗaura musu aure shi da maimouna ya taho da ita ba da duk wannan masifar bata auka masa ba da bai lalata ƴar mutane ba shin yaya shi zai ji lokacin da wani abu makamancin wanda ya aikata ga ƴar yarinyar nan ya faru akan meramar sa ?? Runtse ido yayi yana mai jin nadama na sake lulluɓar sa , yayi nadama kuma yana alƙawartawa kan sa ba zai sake yi ba ,  burkutun da kan ta a yau yana jin wani irin karfin imani da ya jima bai ji irin sa ba akan barin shan ta, ya bar shan burkutun ma , zai yi nesa da duk wasu manyan zunubai tare da yaddar Allah , Yana tsayuwa ya juyo ya dubi yakaka wacce daman shi take kallo , suna haɗa ido ya murtuke fuska , Duk wasu kuɗaɗe da suke aljihun sa na niger da nigeria sai da ya tattaro su  ya zube su akan cinyar yakaka , " maida hannun sa yayi kan Steering ya ɗauke kan sa da nuna alamun yana jira ta fitar masa a mota ne , A hankali yakaka ta ɗago kai tana kallon sa bayan ta kalli kuɗin da ya zube mata su a jiki , kuɗin na menene ? Wani abu zata sayo masa ? toh amma ai waɗannan kuɗin sun yi yawa a sayan abu a dai unguwar nan tasu , anya anya kuwa mutumin nan kan sa ɗaya , ??? Ta wutsiyar ido yaga irin kallon shakkun da take yi masa wanda ya fassara shi a kallon rainuwar yawan kuɗin da ya bata , dan haka ba tare da yace ƙala ba ya sunce agogon hannun sa na ɗanyen farin azurfa da aka ƙawata shi da ƙananun duwatsu masu daraja , ya ɗora mata akan kuɗin ,     Idan kin ka saida shi kudi ne me tarin yawa ," ki gaugawar fita ina da tafiya mai nisa a gaba na ,"   Cikin in-ina yakaka tace Me zan sayo maka da kuɗin toh ? Wani kallon baki da hankali biyamuradi youssouf ya wurga mata ,"   Kuɗin biyan ki taimakon da kika min ne , ki fita ni zan tafi ," Toh ai wannan kuɗin sun min yawa babu abunda zan yi da su ta furta hakan tana mai sauke masa kudaɗen tare da agogon nasa agefen kujerar ta saka kafafu da nufin ficewa a motar kamar yadda yake buƙata ," Wata razananniyar tsawa ya daka mata    Ke bani son sokonci kwashi abun da na baki kiyi tafiyar ki , bana so na sake ganin fuskar ki ," cikin ran sa yana jin takaicin yarinta tare da rashin wayewar ta da take nuna masa a fili wanda yake sa shi ƙara ganin laifin sa tare da zubewar ƙimar sa wai ace kamar shi ya haiƙewa ƴar yarinyar da bata ma kai ga sanin kan ta ba a matsayin mace," wannan abun kunya agare shi dayawa yake ,' Yadda yayi maganar cikin hargagi yasa ba shiri yakaka ta kwashi duk abunda ya bata ta naɗe cikin zanin rufuwar ta da ta tafi da shi a jikin ta jiya ," cikin sauri ta sauka daga motar Bata yi taku biyu ba ya jaa motar a zabari ya bar harabar wajen yana mai jin yadda bugun zuciyar sa ya fara sauyawa tare da iya adadin nisan tazarar da yake yi da yarinyar ," Jiki a sanyaye yakaka ta juyo cikin gida tana mai jin yadda wani abu mai kama da rashin jin daɗin rabuwar su a wannan lokacin yana mamaye ta bata ƙi ba ya zauna tayi ta kallon sa ita dai yana burge ta ɗan gayu ne bugun farko . Biyawa ta fara yi ta ɗakin samy baby domin ta ajiye kuɗin da ya bata amma sai ta tadda ɗakin a datse da kwaɗo ga alama samy baby bata kwan a gidan ba , Zubawa Kuɗaɗen ido tayi tana kallon su kuɗaɗen suna da yawan da ita bata san adadin su ba , ta san suna buƙatar kuɗi ko domin su jaa jari kamar yadda suke da ƙudirin yi , to amma ina zata boye kuɗin ba tare da wani ya gani ba , samy baby tayi niyyar baiwa ajiya ita kuma ga shi bata nan , tana da tabbacin idan har ta shiga da kudin cikin gidam madam saly ta ƙyalla ido ta gan su , raba ta da su zata yi , Hannu ta sa gami da ɗaukar agogon da yake ta ɗaukar ido a hasken ranar hantsi , tsaruwar agogon ya burge ta ko ba'a faɗa mata ba kuma ko da ta kasance bagidajiya ta san wannan agogon mai daraja ne , bare mamallakin agogo da bakin sa ya ce agogon mai kuɗi  dayawa ne ," shin har taimakon da tayi masa ya kai ya bata wannan agogon da dukkanin kuɗaɗen sa ?  Watakila shi ɗin mai kirki ne , Ɗaga rigar ta tayi ta soka agogon a bakin zanin ta tare da gyara ɗaurin zanin gam-gam , Burum aka shigo ƴar kewayayyiyar rumfar katakon da samy baby tayi a gaban ɗakin nata ," A firgice yakaka ta ɗago kan ta tana mai kokarin boye kuɗaɗen hannun ta ," Karaf suka haɗa ido da yagana wacce wannan ne zuwan ta na uku ɗakin samy baby neman yakaka wacce aka tabbatar mata da bata kwana a gida ba kuma babu wanda ya san inda take wanda hakan ya tashi hankalin yagana tare da falmata wacce tun da ta farka ta laluba gidan taji babu yakaka take ta surfa kuka babu ƙaƙƙautawa ," Kai kawo suke ta yi daga waje zuwa harabar gidan da kewayen sa ɗaki-ɗaki neman yakaka , wayam babu ita babu wanda ya ce ya gan ta ma sai mutum ɗaya ne babasho yace tabbas ya ga fitar yakaka tare da wani mutum a daren jiya , Da sauri yagana ta ƙaraso Yakaka ina kika je ? Daga ina kike ? Aina kika kwana ?? Sune tambayoyin da ta jero mata ," Na raka samy baby gidan su ne ! Ina falmata ? Mu ƙarasa ciki ," Tare da shakku yagana ta tsare yakaka da ido , domin sarai ta ga kuɗin da yakaka ta boye mata , uwa uba wani fitinannen ƙamshi da take ji yana tasowa daga jikin yakakar Amma ganin yakakar taƙi nuna mata da kan ta sai ita ma ta bar batun . Ki taho muje falmata taji muryar ki ko ta daina kukan da take ta faman yi tun farar safiya ," Bata ƙarasa rufe baki ba yakaka ta taka da gudu ta nufi cikin gidan , Zaune ta tadda falmatan ta haɗa kai da guiwa a inda ta saba aiki bakin fanfo ga tulin wanke-wanken kofuna da faranten sana'ar su a gaban ta ,"gefe guda kuma kwanan da ta saba sayo musu waina ƴar tsala da suke karin safe da ita ne , a rufe ga alama ko sayo wainar bata yi ba , "ta gaza yin aikin sai kuka ," Da sauri ta ɗago ta tare da rungume ta cikin jikin ta ,'falmata ki bar kuka gani nan na dawo ," Yakaka ina kika je kika kwana ? Meyasa baki faɗa min ba ? Kin sa hankali na ya tashi , yakaka ya zan yi a wurin da bakya nan ? Dan Allah duk inda zaki tafi kike tafiya da ni kin ji ? Naji falmata kuma bazan sake tafiya na bar ki ba ," ta furta hakan tana mai bubbuga bayan ta sigar lallashi ," Yakaka ƙamshin meye ne haka a jikin ki ? Aina kika samu ƙamshi ko a gidan turare kika kwana ? Eh__Ah ah   Unm falmata muyi wanke-wanken kafin rana tayi sosai kin ga mun yi jinkirin fara aiki ,   Toh ai duk ke kika jawo mana ! Madam saly ma ta zo tayi ta masifa tace wai kin fara yawo ,' Tsam yakaka tayi da jin cewar madam saly tayi masifa ," a duniya tana tsoron madam saly , tana matuƙar gujewa bacin ran ta gani take ita ce gatan su ," Kafin rana ta take sun kammala aikin su da suka saba yi har sun fara hidimar abokan cinikayyar su kamar yadda suke a kullum ,"da hakan ya kwaci yakaka daga shan masifar madam saly , dan ita faɗan ta akan harkar ta ne ba wai dan rashin kwanan yakakar a gida ba ! Yo me ya shalle ta ? Babu wanda ya bi ta kan yakaka akan rashin kwanan ta a gida yo bariki ce fa ! ? Yagana ce ma ta so matsawa ta ji toh amma ganin yakakar taƙi bada haɗin kai ta gaya mata inda ta kwanan sai ita ma ta haƙura , har lokacin rabuwar su yayi suka kammala aikin su na yinin ranar , Yakakar ta rako yagana bakin titi kamar yadda suka saba kullum idan yaganar zata koma sansanin su ," Kuɗin da suke dunƙule a hannun ta ta kamo hannun yaganar ta danƙa mata su ," Ga shi yagana ki sayi wani abu nima bani aka yi ," Da sauri yaganar ta ce wa ya baki ? lokacin da take warware ƴan naira dubu guda biyu da yakakar ta miƙa mata su a dunƙule, Wanda na taimakawa ne ya bani ! Taimako ? Wane irin taimako waye shi ? Yagana yanzu ba lokacin hira bane kin ga an kusa rufe hanya kiyi sauri ki tafi sai da safe ! A sanyaye yagana tace   Toh nagode !    Sai gobe ," ta kaɗa kai tayi tafiyar ta zuciyar ta na shakkun ina yakaka ta samu kuɗi haka masu yawa ? Koma menene ita dai tayi farin ciki da kudin da yakaka ta bata koh banza ta toshe wasu daga cikin tarin matsalolin da suke kewaye da ita na talauci ! Akan hanyar komawar ta gida yakaka take tuhumar kan ta meye yasa ta boyewa kowa abun da ya gudana tsakanin ta da mutumin da ta taimaka  ? Oho ita da kan ta bata san dalili ba  , abun da ta gane kawai shine tana jin kunyar bada labarin yadda suka kasance tare ," Dai-dai ta shawo kwanar layin su ƙamshin balangu Barde mai nama ya daki hancin ta ,  tun ba yau ba tasha haɗiyar mugun yawu akan ƙamshin balangun da kullum take wuce wajen da tunanin ina ma ina ma Allah zai kawo wani tsautsayin da zai gifta ya sa tukubar balangu barde ta tuntsira ita kuwa ta daka wawaso ,! Saboda ba ƙaramin ran ta biyawa yayi da balangun nan ba ,! Rabon ta da nama shekarun da ƴan yawa ,' to su da suke ta abinda zasu ci su kori yunwa ina su ina nama ,"kayan wadata " Yau da take jin ƙugun ta danƙam da kuɗi , tana shaƙar ƙamshin ta saki hannu ta bishi , har cikin ƴar rumfar barde , Cikin nutsuwa ta gaida barde Ya amsa mata haba-haba irin na ƴan kasuwa ," Ta miƙa masa gudar ɗari biyar ɗin da ta ciro daga ƙugunta , Na nawa za'a yanka miki Ƴan mata ,?" Na dukka ! yakaka ta furta hakan tana mai gyara tsayuwa jin kan take a sama ," naman ɗari biyar ai ba kusa ba ," Take barde ya washe baki ya fara yanko naman daga gefe-gefe yana kachal-chala shi akan ƴar takarda neɗe nama ,' Da sauri yakaka tace a ah ba nan zaka yanka min ba nan nake so wuri mai nama-nama da mai ɗin ," ta nuno wurin da yafi ko'ina sheƙi a jikin naman yana ta nason mai da yaji ," Au to toh bari a yanko miki nan ɗin,"( kuturu da kuɗin sa ai alkaki sai na ƙasan langa ) Ƙarbar balangun tayi bayan ya naɗe mata yaji a wata ƴar takadda daban ya haɗa ya sa mata cikin leda ," A ci daɗi lafiya ƴan mata ! Tun a harabar gidan ta fara ƙwallawa falmata kira wacce take zaune daga gefe a babban filin , inda ɗan asharalle ya baje gangunan sa da shi da yaran sa suna ta bugun ganguna ," kalmomi ne na batsa ake rera waƙar da su , mata Sun shiga layi kowacce tana nuna ƙwarewar ta a fannin girgiza kwankwaso tare da juya sassan jiki ,' mazan da suke zagaye da su suna kallon su tare da yin eho har wasu suna faɗawa filin su yi wa budurwar su ko wacce ta birge su liƙi ,"  Ta ko'ina jama'a ne birjik a harabar masu cha-cha da karta nayi masu hira  musun ball suna fama ,! Kamo hannun falmata tayi suka shiga daga ciki sashin madam saly inda babu yawaitar mutane sosai saboda mafi yawa suna filin chasu ," A gefe ta zaunar da falmata kan wani ɗan dutse , ita ma ta zauna gami da warware ƙunshin naman ta ɗauko ƙatuwar tsoka bayan ta ɗan ɗangwalo yaji ta nufi bakin falmata da shi , wacce tun da aka buɗe naman ƙamshin sa ya buge ta yawun ta ya tsinke ," Ungo falmata buɗe bakin ki kici nama ," Unm unm yakaka waye ya baki wannan naman mai daɗin tsiya  ?, cewar falmata a lokacin da take ƙoƙarin haɗiye na bakin ta ,! Ni na sayo mana falmata , Yakaka ta furta hakan tana mai sake nufar bakin falmatan da wani yankan Chak falmata ta tsaya da taunar wanda yake bakin ta . Aina kika samu kuɗi yakaka ? Wanda na taimakawa jiya ne ya bani ! Waye shi , ? Wani ne baki san shi ba falmata nima kuma ban san shi ba , taimakon sa kawai nayi ya tafi kuma yace ba zai sake dawowa ba , ta furta hakan tana jin wani yanayi marar daɗi yana taso mata kalaman sa na ƙarshe suna mata amsa kuwwa cikin kunnen ta ," Bana son na sake ganin fuskar ki ,"        Kenan ba zai dawo ba ,      zuciyar ta ta aiyana haka! Kai amma yana da kirki ! Cewar falmata lokacin da zaƙin naman yake ratsa ta ,"    yakaka bata samu zarafin amsa mata ba saboda zuciyar ta da tayi ƙunci ," a take ta ji ta daina jin garɗin naman dan haka ta miƙe gami da cewa falmata tana zuwa ," ta ci naman iya cin ta . Shagon sayar da kayan masarufi da amfanin yau da kullum ta tafi wanda bashi da nisa sosai da gidan su , Ta miƙa dubu ɗaya tace a bata manyan jakar bacco guda biyu , da sabulun wanki guda uku da na wanka sinki ɗaya da kuma omo babbar jaka ," ɗan jim tayi tana tunanin bayan su kuma me yakamata ta saya ?    Har zata ƙarbi sauran chanjin ta idanun ta suka sauka akan jerin ƴan mukullaye da suke jikin wani ɗan karfe ," wani tunani ne ya faɗo mata A bani ƴan mukulli ƙanana guda biyu ," Ta haɗo sayayyar ta ta komo gida kai tsaye ta wuce ɗakin da su falmata ke kwana , ta jawo yagaggen jakar bacco wanda suke tara kayan su a ciki ita da falmata , Ta fiddo dukkanin suturun su ,"babu laifi yanzu suna da ƴan kaya ," Ta warware sabbin bacco , ta ware kayan falmata ta jera mata su tsaf a ciki bayan ta gyara ninkin ta ɗauki ɗaya daga cikin ƴan mukullin ta kama bakin zif ɗin ta sarƙafa shi ta bame ," Ta warware ɗayar bacco ta buɗe ciki , Ta fiddo kuɗaɗen ta tare da agogon da ya bata ta saka kuɗin a cikin bacco , ta riƙe agogon a hannun ta , ta tsura masa ido , " kyakyawar fuskar sa tana mata yawo a zuci , ƙamshin da yake manne da jikin agogon ya mamaye mata hanci , ta ji wani irin nishaɗi tare da shauƙi suna huda ta, ina ma ina ma da ace har yanzu suna tare tana kallon sa tare da shaƙar ƙamshin sa ? , a hankali ta kai agogon hancin ta ta sunsuna gami da rufe idanun ta , shi ma'abocin ƙamshi ne kome da ya dangance shi ƙamshi yake hatta kuɗaɗen da ya bata ƙamshin sa suke ," a hankali laɓɓan ta suka motsa cikin yaren ta tace,"Bature kam silum ," ( baturen baƙaƙen fata ,) Motsin da ta ji yana nufo ɗakin ya sa tayi saurin ajiye agogon a gefen kuɗin ta fara jera kayan ta bisan su ," ****************** Iya adadin nisan da yake yi da yarinyar iya adadin daɗuwar rikicin da yake ji cikin zuciyar sa tare da gangar jikin sa baki ɗaya ji yayi masifar da yake zaton ta ƙare tana sake taso masa ,' Addu'o'i ya shiga yi iri-iri idan ya kama wannan ya gama ya kamo wancen , Ga mamakin sa kamar sake ƙaruwa lamarin yake domin zuwa yanzu karfi da yaji yake jin ana son sarrafa gangar jikin sa ya juya kan motar ya koma wurin ta , kamar yadda zuciyar sa ta riga tayi tsalla ta koma gare ta , " Karfin addu'ar da yake yi ita ta duƙushe tasirin ko ma menene , har ya samu ya kawo inda suka yi masauki a bakin dajin , Bai kula kowa ba duk kuwa da gaisuwar ban girman da suke yi masa ta hanyar ƙamewa su sara masa , Kai tsaye ya shiga bayin sa ya ɗauro alwala , ya dawo cikin tantin sa ya sauke farillar sallar asubha da take kan sa , Yana idarwa baiyi ƙasa a guiwa ba ya ɗauko alqur'anin sa ya buɗe murya cikin nutsuwa ya fara tilawa , A hankali nutsuwa tare da amincin da suke tare da alqur'ani suka fara ratsa shi tare da yin tasiri ga wannan yanayin da yake tunzura shi ,' Jingina kan sa yayi da jikin karfen tantin nasa lokacin da yaji wani irin bacci mai nawi yana son fusgar sa ,' Ƙiran wayar sa shi yasa shi buɗe idon sa daga son yin bacci da yake ,' Ami Tafeêdah Shine sunan da ya bayyana à fuskar wayar !  Da rashin kuzari biyamuradi ya amsawa tafeedah sallamar sa, bayan nan suka ɗora da tambayar lafiyar juna ," ?   Ɗan ouwa da dama kou ? meke damun ka ? lalle cikin yanayin ka akwai damouwa yi gaogawar sanar da ni ? Shiru youssouf yayi , yasan tafeedah yayi masa farin sani , yana kuma iya karantar kowanne irin yanayi yake ciki ," to amma baya jin zai iya faɗa masa damuwar sa, toh yace me wai ??   Ya sake dulmiyewa cikin alfasha bayan wanda tafeedan ya san yana aikatawa, ya ƙara da wata ??    Ɗan ouwa bani jin daɗin jiki na ne kawai , ciwon kai na damu na ,!   Babu kome ka ɗaure abokina idan har ka cigaba da ƙaurace mata a hankali ahankali duk wasu yanayi masu wuya da kake shiga idan baka sha ba zaka ji ka daina jin yanayin , sannan ka sake dagewa da addu'a . Uhum ita ce kawai kalmar da youssouf ya furta     Da ace tafeedah ya san abun da ya aikata da babu abun da zai hana abotar su ta samu tangarɗa Nagode ! Cewar youssouf Daga haka suka ɗan yi hira sama-sama , ganin youssouf ɗin bai tare da nutsuwar sa sosai ya sa suka yi sallama tare da sake ƙara masa ƙarfin guiwar gujewa burkutu ! Yadda youssouf ya ga rana haka ya ga daren yau ," tsafi gaskiyar mai yin sa ne ," Da ita yake son kasancewa a yanayi irin na daren jiya , rashin samuwar hakan a gareshi ya haifar masa da masifaffan ciwon ciki da amai bayan masifar da yake ji a ruhi da ƙwaƙwalwar sa , ji yake kamar ya zura da gudu yayi ta gudu har ya tadda ta , ko kuwa dai yayi fiffike ya sauka gare ta a cikin daren ," Shajaran majaran ya wayi garin a halin jikkata , da ya sanya tilas likitocin da suke abokanan aikin su suka shiga bashi taimakon gaggawa , ƙarin ruwa zuwa magunguna ," ba laifi lafiyar jikin sa a zahiri ta dai-daita amma shi kaɗai ya san halin da yake ciki a ruhin sa , Zuwa azahar ya ɗan ji karfin jikin sa , dan haka yayi wanka ya ɗau shiri , zuciyar sa ta gama samun galaba akan sa tare da taimakon shaiɗanin da yake tare da shi yana bibiyar sa tare da ingiza shi , Karfe biyar na yammaci tayi masa dot a ƙofar su yakaka ,' Kan sa tsaye ya shiga gidan yana mai fatan cin karo da ita kawai su tafi , sai dai kuma inda gizo ke saƙar shine , shi fa bai wani tantance da kamannin yarinyar nan ba ," alhali kuma ya gama shawartar kan sa akan ya tsaya tare da ita kawai ta dunga biya masa buƙatar sa tun da shi ne mutum na farko da ya fara sanin ta ," shi kuma zai ɗauki duk wasu hidindimun ta har sai zuwa lokacin da ya fita a masifar da ya faɗa ,' Da wannan tunanin ya sanya kai cikin rumfar madam saly , ya tadda babu mutane dayawa mafi yawa suna wurin chasun da ya gitta a yayin shigowa ," Wuri ya samu daga gefe ya zauna , zuciyar sa na fatan ganin ta kamar yadda yake yawata idanun sa akan ƴan matan da ke kai kawo ta gaban sa , baki ɗaya bai ga fuskar ta ba acikin su , Ina take ? Ya san fara ce tas , bayan haka babu abun da zai ɗorar na daga suffar ta ,' Yagana ce ta ratso ta cikin rumfar cikin shirin tafiya gida, yakaka biye da ita da nufin yi mata rakiya ta dawo ta ƙarasa aiyukan da take kaiwa har dare tana yin su daga wannan zuwa wancen ! Tana sanyo kai ta ji ƙamshin sa ,' tabbas wannan ƙamshin "bature kam silum " ne , a take bugun zuciyar ta ya sauya tare da wata kewar sa mai tsanani da ta taso mata Ina yake !  Tambayar zuciyar ta Tun da suka bullo ya gan su , a take zuciyar sa ta shaida ta tabbas ita ce abar kwaɗayin sa ita ya zo nema ,! Hankalin ta ya rabu biyu ɗaya yana ga hirar da yagana ke yi mata ɗaya yana ga son gano inda yake , dan haka bata samu nasarar ganin sa ba har suka zo giftawa ta gefen sa ," Ganin zata wuce shi ya sa shi miƙa hannu ya kamo hannun ta ," Da sauri ta juyo domin ganin waye ne ,"duk da cewa an saba yi mata haka ," Idanun su suka sarƙe cikin na juna kowannen su ya gaza ɗauke idanun sa , a yayin da suke fassara kallon da suke yiwa juna a zuciyoyin su ," Kallon da yakaka ke bin biyamuradi kallo ne na nayi kewar ka , na kuma yi farin cikin sake ganin ka , Yayin da take fassara kallon da biyamuradi yake jifan ta da shi a nufin.!    Gani na dawo ki sake taimaka min .,'     Zan taimaka maka ta ƙudurce cikin ran ta ,!   Har yagana tayi ɗan nisa ta waiwaya bata ga yakaka ba dan haka ta dawo da baya nan ta tadda ta suna kallon juna da wani mutum da bata kai ga sanin sa ba , da ido ta bi hannayen su da yake manne ,! Dafa kafaɗar yakakan tayi ganin irin shagalar da tayi ,bata san ma ta zo wurin ba Da sauri yakaka ta zame hannun ta daga cikin na biyamurdi ," Ina zuwa ,' tace da shi ! A bakin kofar shigowa ainahin gidan ta dogare yagana  zan koma daga nan kin ga ana jira na ! Da ido yagana take bin ta cikin ranta tana mamakin farin ciki tare da murnar da yakaka take yi wanda kafin fitowar su a ɗazu babu shi,' A karo na huɗu ta sake tambayar ta Wai yakaka sai tambayar ki nake kin share ni waye wannan ɗin ko ƴan uwan ku ne ? Bature kam silum ne ,    Ɗan uwan mu ne Daga haka ta juya da sauri har tana haɗawa da ɗan gudu ta koma ciki , Ta bar yagana da mamakin ta fal cikin rai , " bature kam silum' ta maimata sunan ,! sashi guda na zuciyar ta yana shakkun ambaton sa da tayi da ɗan uwan ta , kai wannan daga gani ba yaren mu bane ! Da murmushi akan fuskar ta ta ƙaraso gaban sa ,   Ki kimtsa ki taho mu tafi ,kadda ki ɗau lokaci Ya furta hakan yana mai ɗauke kan sa daga kallon ta ya mayar ga agogon hannun sa ," Kalmar kimtsawa tai mata tsauri wurin fahimta , amma da yake tana jin sa cikin zuciyar ta , sai ta kintata ta  hasaso abun da yake nufi , dan haka ta shige ciki ,"     Ƙasa-ƙasa ya bi takun kafafu da kallo wanda yake halin sa ne kallon ƙasan ido ,"         nan ya hango dauɗa tare da taron kursashin da yake danƙare ƙasan kafafun ta . Cikin sauri ya ɗauke kan sa ! A gurguje ta shiga ta ɗibi ruwa tayo wanka , ta dawo ɗakin su larki ta hau shiri ," falmata wacce take zaune shiru kamar yadda yake al'adar ta ce killace kan ta wurin da babu kowa tayi shiru ,"   Motsin da taji an taɓa musu jakar kayan su , ya sa takai hannu tana kamo jakankunan nasu ,"     Waye anan ? Yakaka wacce ɗoki ya sa bata ko yi sallama ba bare tayi wa falmatar magana , tace,           Nice fa falmata nah ," Aiyo yakaka na , to ai baki min magana bane ! Yau har kin gama aikin ne ? Ban gama ba falmata , Mutumin shekaranjiya ne ya dawo yana so mu je na sake taimaka masa ," Zuruf falmata ta miƙe nima zan biki yakaka ,! Tsam yakaka tayi ta bar ƙoƙarin sanya kayan ta da take yi , Ta taso ta zo ta kamo hannuwan falmata ,"    Falmata na kiyi hakuri ki zauna har naje na dawo , kin ga aikin da nake yi masa mai wahala ne baza ki iya ba , kuma yau bazan kwana ba , anjima kaɗan zan dawo kin ji ?    Da kyar ta shawo kan ta ta yadda zata jira ta tare da alƙawarin baza ta kwana ba zata dawo , da haka ta kammala shiryawa cikin wata atamfar cote d'ivoire ruwan zuma mai cizawa da aka yiwa ɗinkin riga da siket , duk cikin ire iren kayan da samy baby tayi mata kyautar su ne da basu sha jiki sosai ba ," wani turaren da samy baby ta bata lokacin da take menses ta ce ta dunga shafawa a jikin ta ,"shi ta ɗauko ta mutsittsika ,"    Fes tayi kyau ta ɗaura ɗankwalin ta shigen yadda ta ga samy baby na yi , bata sanya gyale ba domin bata da shi kuma ka'idar gidan madam saly ba'a yawo da mayafi .! Wannan karon a tsaye ta tarad da shi ya saka hannun sa ɗaya cikin aljihun wandan sa , da alama tsumayen ta yake cikin ƙaguwa ," Babu laifi a idon sa tayi kyau , duk da cewa shi ba wannan bane ya dame sa , Sai dai tana matsowa kusa da shi ya ji wani ƙamshi marar daɗi a hancin sa yana tashi daga jikin ta , sam ƙamshin  bai masa ba ,! Juyawa yayi ya fara taku ba tare da yace da ita ƙala ba ," Zungui-zungui ta bishi a baya , Duk yadda yaso ya Daurewa ƙamshin turaren dake tashi a jikin ta ya kasa , sosai yake jin wani yanayi marar daɗi a cikin ƙamshin  , shi mutum ne mai tsananin tsafta da ƙyanƙyami sam bai son wani abu da yake da alaƙa da ƙazanta ," Dan haka lokacin da suka daidaita akan titi ,ya ɗan juyo da ganin sa kan ta ,"     Ki gwouda mini hanyar les salons !     meye kuma Les salons, ?  ita hausar sa gaba ɗaya wahalar fahimta take yi ma ta ,"      A takaice ta amsa    ban san wajen ba ! Wani wuri ya samu a gaba kamar super market ya tsaya shaguna birjik a wurin , Mayuka tare da sabulai zuwa turaruruka na mata , masu kyau da tsada ya jida , Ya koma banagare kayan sawa ,"shi ba wani sanin size ɗin ta ya yi ba dan haka ya ɗauki dogayen riguna baƙaƙe biyu , A wurin biyan kuɗin ya tambayi Cashier wurin salons , nan ya masa kwatance na wani shahararren wurin gyaran jiki da yin kwalliya , TaTa saloons da yake kan titin danboa . Ya ajiye kayan a kujerar baya ya zo ya tada motar ba tare da yace da ita ƙala ba , ita ma kuma tayi shiru bata magana sai satar kallon sa , Tata salon babban wurin gyaran gashi , ƙafa da ƙumba , yin kwalliya da gyaran jiki ,  zuwa sayar da turarurrukan arabs masu kyau da ƙamshin sanyaya rai ,suna da gyalalluka na yayi masu matuƙar kyau da inganci . Hajiya ruma mamallakiyar shagon mace ce mai karamci wacce ta san harkar kasuwa dan haka take girmama abokan cinikayyar ta , ( Allah ya ƙara ɗaukaka ƴar ƙanwa ta ) Sun ci sa'ar tarar da ita da kan ta , inda tayi musu tarɓar girma tare da ruwan gora da lemun gongoni ," nan youssouf yace ayi wa yakaka gyaran jiki tun daga salons zuwa pédicure , kai har wanka ma ayi mata ,! . Aka sa masa kuɗi ya biya . Nan aka shiga da yakaka wani ɗan ɗakin da ya wadata da fitilun haske ,' Suka fara aikin su , goge nan wanke chan , dirza nan shafa wannan goge wancen , har dai suka samar da yadda suke so a jikin yakaka , duk da cewa su da kan su sun yi mamakin irin dauɗar da take danƙare a kowanne lungu da sakon jikin yakaka , ,misalin karfe takwas na dare suka fito da ita , tayi kyau ba kaɗan ba , ɗan nude makeup ɗin da suka mata ya sake fiddo da zallar manyan kyaun da take da shi , jikin ta sanye da ɗaya daga cikin dogayen rigunan da ya saya mata ,sun yi mata naɗi da gyalen rigar bayan sun tara mata gashin ta mai rangwamen duhu sai tsanananin laushi da tsawo a tsakiyar kan ta sun kama mata shi da roba ," , ita da kan ta jin kanta take kamar ba ita ba kamar an sauya ta , wani irin nishaɗi ne yake huda ta , ƙamshin da yake mamaye da sassan jikin ta yana bata wani irin farin ciki na musamman, tsafta tayi a rayuwa ," ita kuwa me bature kam silum zai biɗa a wajen ta da baza ta iya masa ba ? ai babu ! Da ido yake bin ta da kallo lokacin da suka fito , duk da cewa idanuwan sa sun saba ganin kyawawan mata daga bangarori daban daban na duniya , amma kwarai irin nata kyaun ya burge shi ," daga inda yake yana jin tashin ƙamshin ta ," Da hakan ya sa shi sakar mata murmushi da suka haɗo ido , a karo na farko da yakaka ta ga murmushin sa wanda yake ƙarawa fuskar sa haiba , nan take ta washe gajerun hakoran ta da suka sha wanki tana maida masa da martanin dariya , tsintar kan ta tayi da tambayar sa ,"      Nayi kyau ko ? Murmushin bai gushe ba akan fuskar sa ya haɗa yatsun sa biyu babban da mabiyin  sa ya mata alamu da kinyi kyau sosai ! Hannun sa ya miƙa mata ta ɗora nata akai ya ja ta suna mai ficewa a shagon   ma'aikatan shagon suka bisu da kallon sha'awar da suka basu ,"Cikin ran su suna aiyyanawa ma'aurata ne irin sabon auren nan har wata ƴar gaza gani daga cikin su ta tanka ," perfect couples" Kwanakin da suka biyo bayan wannan ranar biyamuradi youssouf da yakaka zama suke irin na masoyan ma'aurata , babu wata rana da ta tsallake musu da basu kwana tare ba . Yayin da biyamuradi yake fidda kuɗi yana mayar da yakaka irin macen da yake so , ƴar hutu ƴar gayu mai tsafta , tata salons ya zama wurin zuwan su , bai jin ƙyashin kashe mata kuɗi tare da bata farin kuɗin tsurar su domin ta biya wasu buƙatun , har ƴar ƙaramar waya ya saya mata , wanda yake amfani da ita wurin kiran ta idan ya zo ɗaukar ta ," a yanzu burkutu guzurin ta yakaka take yi masa , har ɗakin da suka mayar na kwanan su a garki Guesthouses , Yakaka kuwa sau da kafa take bin biyamuradi youssouf cikin dukkanin buƙatun da ya zo mata da shi bata iya kuya masa baya , tana bashin haɗin kai tare da juriyar ɗaukar bukatun nasa ," A yanzu aikin gidan madam saly ya ragu a kan ta , saboda yadda biyamuradi da ita kan ta yakakar suke sakarwa madam saly kuɗi , wacce a rana ta biyu da yakaka ta sake bin biyamuradi suka kwana alhalin bata gama mata aiyukan ta ba kusan raba dare tayi tana zagin yakakar tare da shan alwashin a gobe gobe zata kore su , Da hakan ya sa falmata kwana tana kuka ita ba kome yafi bata mata rai ba irin kalmar "ƙaramar karuwa sabuwar yar iska ," da madam saly ta danganta yakakar da shi ba ," cikin muryar kuka ta dunga maimaita kalmar    Yakaka na ba ƴar iska bace    Yakaka na ba ƴar iska bace Ƙasa-ƙasa yadda madam saly bata jiyo ta ,' tsaf ta gama kintsa musu jakar kayan su tana jiran gari ya waye yakaka ta dawo su kama hanyar su," Sai dai abun da ya ɗaure mata kai washegari bayan dawowar yakaka gidan tayi ta kasa kunne ta ji hayaniyar madam saly tana zagin su tare da kora kamar yadda tayi rantsuwa , " sai taji tsit , sai ma jin madam saly tayi ta zo har cikin ɗakin nasu tana bawa yakaka wani abu tare da shaida mata idan har ta sha shi da madarar ruwa ko nono , ba ƙaramar kyauta saurayin ta zai yi mata ba ƙila ma ya bata "mota ," Saurayi kuma yakaka ?   Wanne saurayi ? Tambayar da falmata ta jefawa yakaka kenan , bayan ta cika bakin ta da donut,  wacce ita ma yakakar ta toshe mata baki da kayan maƙulashen da biyamuradi ya ciko mata manyan ledoji da su ,lokacin da ta so tada bori akan kwanan da yakaka ta sake yi a waje ,!     Ba saurayi na bane wanda nake taimakawa ne ,"     Wai yakaka wane irin taimako kike yi masa da har yake baki kayan daɗi haka ? ga turare mai ƙamshi da kika ce ya baki har da su mai ," to kawai mu koma gidan su mana mu dunga yi musu aikin tare koh ba taimakon sa kike da aiki ba ? Cikin diriricewa yakaka ta ce,"     Ba-ba ba agidan su muke aikin ba a wani waje ne ,falmata kiyi zaman ki anan tun da ni ina zuwa nemo mana , kuma ina samo mana kuɗi , kin ga tunda kuɗaɗen dayawa idan suka taru har ɗaki zamu iya kamawa mu bar gidan nan , mu kama sana'a a hankali a hankali muna neman su maman mu ko ?  Take falmata ta hau murna jin za'a nemo maman su ," nan dai ta hakura zata dunga zama yakaka ita zata dunga zuwa sabon aikin da ta samu ! Haka kwanaki suka jaa har yau da suke kwanaki goma sha huɗu da fara tarayyar su , zuwa yanzu yakaka tayi nisa cikin makauniyar soyayyar biyamuradi bata ji bata gani wata irin mahaukaciyar soyayyah take masa da bata ƙi ba su tabbata har abada a tare , Ta bangaren biyamuradi kuwa shi tun farko babu batun so atsakanin sa da yarinyar , hasalima ya ɗauke ta ne kawai a matsayin mai bashi maganin cutar da yake ganin ta kama sa a kwanakin nan na jarabar mace , wanda a yanzu kuma yake jin ya fara samun sauƙi domin a ƴan kwanakin nan yanayin da yake ji mai tsanani a duk ranar da bai kusance ta ba ya ragu , dan haka zuwa yanzu ya fara jin zai iya daina harkar gaba ɗaya tunda daman dole ce ta sanya shi farawa ,( a cewar sa ) A yau yayi niyyar sallamar yarinyar da ƴan kuɗaɗe masu tsoka domin yau idan ya koma daji ba zai sake fitowa kwana kusa ba zai maida hankalin sa kachokam kan aiki , giyar da kan ta zai gwada barin ta na kwana biyu , Daga wanka ya fito jikin sa ɗaure da towel , kai tsaye ya nufi ƴar wadrobe ɗin da take ɗakin ya fiddo da mai tare da mataji ,( comb ) ya shafa mai tare da taje ƴar sumar sa da bata cika yawa ba ,  , ya jawo ƴar ƙaramar jakar matafiya da yake sako kayan sa a ciki shiga ɗaya idan zai shigo gari ya fiddo kakin sa na soji ya sanya ya fesa turare tare da ɗaura agogon sa , kayan jikin sa da ya cire wanda yake riga long-sleeved da dogon wando , ya ɗauka ya mayar cikin jakar tare da haɗo ƴan sauran tarkacen sa duk ya zuba a ciki , Ya samu wuri ya zauna a gefen gadon ya jawo takalman sa mahaɗin kayan sa yana ɗaurawa a kafar sa , Duk abun da yake yakaka wacce take shirye tsaf a kishingiɗe a gefen gadon tana bin sa da kallon so da ƙauna haɗi da burge ta da duk wani motsi na sa yake , " Tunani take ina ma ina ma ace wannan kyakkyawan mutumin da har yau bata kai ga sanin sunan sa ba duk kuwa da kusanci mafi girma da suka samu a tsakanin su , ina ma da zai AURE TA , ?    Da ita kuwa ta gama jin daɗin rayuwa tare da nasarar rayuwa , Ɗago kan sa yayi ya kalle ta , ɗan gajeren murmushi yayi mata     Yaya irin wannan kallo haka ƴan mata ? Kayi kyau bature kam silum ," amma ina ta tambayar ka meyasa kai kayan ka ba irin na sauran sojoji ba , baka bani amsa ,"  A  takaice ya amsa mata saboda ni ba sojin ƙasar ku bane ,"     To inane ƙasar ku ?      Wani wuri ne mai nisan gaske ! ,"ya amsa mata   Wallet ɗin sa ya ɗauka ya fiddo da dukkanin kuɗaɗen ciki , da suke sabbin ƴan dubu ɗai ɗaya , " ya tako ya zagayo ta bangaren da yakaka take ,   Kamo hannun ta yayi tare da ɗora mata kuɗin ,"   Ƴan mata ,( kamar yadda yake kiran ta tun haɗuwar su a zahiri ya manta sunan ta bai kuma taɓa damuwa ya sake tambayar ta sunan ta ba toh ina ruwan sa da sunan ta ? Amfanin me sunan zai masa ? )     Ni zan tafi yau kuma bazan dawo nan kusa ba saboda yanayin aiki na , ƙila na dawo cikin sati biyu masu zuwa ƙila sai cikin wani watan watakila kuma .... Sai ya ɗan yi shiru  tare da duban fuskar ta ," Wacce tunda ya fara bayani idanuwan ta suka cika da ƙwalla , wani irin bugu zuciyar ta take yi , Zame hannun ta tayi kuɗin suka sauka akan katifar ,"           "ka bar kuɗin ka bature kam silum ba sai ka biya ni ba , ni dai dan Allah kar kace baza ka dawo yau ba , ka dawo dan Allah ni ko baka bani kuɗi ba zan taimaka maka kamar kullum , akwai wasu sauran kuɗin da kake bani ma ina tara su duk zan dawo maka da su ni dai dan Allah bana so na daina ganin ka , idan bana tare da kai zuciya ta bata min daɗi , na saba da kai . tun da ta fara magana yake bin fuskar ta da kallo wacce kafin ta kammala ta jiƙe da ruwan hawaye , wani irin tausayin ta ne ya kama shi , tausayi mai tsanani , ya fahimci yarinyar ta faɗa a tarkon son sa , wanda shi kuma sam bai so hakan ba domin kuwa a zahiri bata da gurbi cikin rayuwar sa ko kaɗan , " shi kuwa ina zai kai ƴar talakawa marar galihu irin wannan yarinyar toh ya kai ta ina ? Masarautar su ? Ai auren ɗan sarki sai ƴar sarki idan kuwa ba ita ba toh sai fa ƴar manyan attajirai ," kai shi bai taɓa ɗaukar ta da wani matsayi ba ma da ya wuce macen da yake biya ta gusar masa da sha'awar sa , bata da wani banbanci da sauran karuwai !   Duba ƴan mata ," ni akan aiki na zo ƙasar ku , batta kasancewa kullum mu zauna tare , ki ɗauki kuɗin ki riƙe a hannun ki zasu miki amfani watarana , ni akan hanya nake ," ki manta da ni kiyi rayuwar gaba har yanzu ke yarinya ce kin ji kou ? Tashi mu tai na sauke ki gida . A motar ma share hawaye yakaka take sosai take jin ciwon barin ta da zai yi , yace wai ta manta da shi , anya ? Ita ta san baza ta iya mancewa da shi ba ," ya samu wani irin gurbi mai girma ya kafa kan sa cikin zuciyar ta ,"  kiran wayar sa shi ya katse shirun su , samun waje yayi ya tsayar da motar a gefen hanya , " nan ya amsa wayar     Kira ne na gaggawa ake yi masa daga sansanin su na soji ! Da sauri ya buɗe murfin motar da hannu yake yiwa yakaka alama na ta sauƙa masa a mota ," Jikin ta a sanyaye ta sauƙa tana gama ficewa a motar ya ja murfin da ƙarfi ya harba motar bisa titi a guje .' tsumu ta tsaya a gefen hanyar tana sake kallon kuɗin hannun ta ," kome bai mata daɗi wani irin ɗaci take ji daga ƙasan ran ta yana taso mata ,   Matsawa tayi jikin wata mota da take tsaye a gefe ta jingina jin da tayi tsayuwa na neman gagarar ta ," kuka take son yi so take ta samu wuri tayi ta kuka ko zata ji saukin abun da take ji a ran ta , da gaske ya tafi bazai dawo ba ? ko wasa yake yi mata ? Tun kafin ya tsallako titin daga ɗan shagon da ya tsaya ya saya kayan marmari a gefen titin ,  hasken ta ya dalle masa idanu , amma kasancewar sa mai tsananin kamun kai da nutsuwa babu ruwan sa da harkar mata (irin yadda samarin yanzu suke )  ya sa yayi saurin ɗauke kan sa , Har ya ƙaraso jikin motar da take jingine da take mallakin sa ce bai sake kallon inda take ba ," Murfin motar ya kama zai buɗe sannan ya juyo ya dube ta ,"     Baiwar Allah zan ɗauke motar daga wurin ,!     Ko gizau bata motsa ba   Ɗan tsaki ya ja marar sauti , wasu matan dai basu da kamun kai dubi wannan yadda ta zo ta dogare a bakin titi duk masu wucewa idon su akan ta . Ya sake maimaitawa da ɗan karfi ,    Zan ɗauki motar nace baiwar Allah a hankali ta juyo da fuskar ta inda take jin tashin muryar sa , kamar ta san muryar ,!    Kallon juna suka yi ido cikin ido , Tsai yayi yana kallon ƙwarar idon ta , shin ita ce ne ko ba ita bace ? Ƙwarar idanun ta suna tabbatar masa ita ce wacce ya shafe fiye da watanni biyu yana neman ta tsakanin sansanin su da zagayen kasuwa ,wacce a karshe ƙawar ta tace sun gudu sun bar garin ," sai dai kuma yanayin shigar ta da gogewar da ya hango tare da wannan suna ƙarya ta masa ita ce , wacce ya sani ai ƴar ƙauye ce ƙazama , wannan kuwa ƴar birni ce wayayyiya kuma ƴar gayu ," kai sai dai kamanni , ," da sauri ya saita kan sa daga ruɗanin da ganin kamar wacce yake bulayin nema ce ya sanya shi ,"   Ya ɗaure fuska gami da maimaita maganar sa ta farko cikin ƙosawa ," A hankali ta janye jikin ta daga motar , "     Ta gane shi sarai shine likitan da ya sha taimakon ta tun farkon zuwan ta garin ,"! Sai dai halin da zuciyar ta ke ciki a yanzu babu damar da zata tsaya yin magana da kowa ko da kuwa kalmar gaisuwa ce , domin tana buɗe baki kukan da take yi a zuci ne zai fito fili , dan haka ta ɗauke kan ta ,' ta matsa bakin titin sosai domin tarar adaidaita ya kai ta gida tayi jinyar gangar jiki da ruhin ta da tun yanzu suka fara kewar bature kam silum ," Tana matsawa a jikin motar ya shiga gami da jan motar sa , a cikin ran sa yana mamakin al'amarin hatta tafiyar su iri ɗaya ya furta hakan a fili yana sake leƙen ta ta jikin madubin motar ,"  gefe guda na ran sa ƙaunar yarinyar da har yau bai ko kai ga sanin sunan ta ba yana tasowa , ya so ƙwarai ya nemo ta , domin a ranar da suka bar asibiti ita da ƙanwar ta ba ƙaramin damuwa ya shiga ba , so yayi ya ɗauke su ya kai su gidan sa inda yake zama tare da mahaifin sa da ƙannen sa ya ɗau nawin su ya inganta rayuwar su ita da ƙanwar ta , ya sha wahalar neman su da kwatance su a sansanin su dakyar aka samu wacce ta san su aka ce tare suka zo , tashin farko da ya tambaye ta game da su tace da shi YAKAKA DA FALMATA SUN BAR GARIN . Assalamu Alaykum  my dear sisters ! How are you guys doing today  ? I hope everything is well ? Please don't delete comments because I didn't reply straightaway . I hardly get time to come frequently , but I do dedicate some time every now and then to reply to y'all Insha Allah  ! I hope you guys enjoyed this chapter  ??  buckle up cause chapter twenty is going to be a sadness one!  LET ME KNOW WHAT YOU GUYS THOUGHT ,PLEASE  COMMENT , VOTE, AND SHARE WITH YOUR FRIENDS AND FAMILY.     THANK YOU .               [6/24, 10:59 AM] +234 701 013 7848: MAFARI ....... Hargitsin Rayuwa umm"muaz 20 Yakaka tana shiga gida Kai tsaye sashin samy baby ta nufa , ta ci sa'ar samun kofar ɗakin ta a buɗe kai tsaye ta danna kai cikin ɗakin idanun ta a rufe da ruwan hawayen da yake ambaliya ," Zube guiwar ta tayi a ƙasa tare da yin jifa da kuɗaɗen hannun ta suka tarwatse a tsakiyar ɗakin ,hannuwan ta biyu ta sa ta rufe fuskar ta lokacin da take sakin kukan da yake cin ta a zuci . Sautin kukan da yayi sanadiyyar tashin samy baby a firgice daga baccin tofon girar da take shaƙa ,"  Da sauri ta zo ta kama ta Yaks meye ya same ki ? Duka aka miki ? Ko meye ? Kusan ba a hayyacin ta ba ta riƙo hannun samy baby ,   Dan Allah ki ce masa ya dawo kar ya bar ni , idan bana ganin sa mutuwa zan yi , kin ga nan ,"ta ɗora hannun samy baby akan zuciyar ta ,"ciwo take min ina jin wani abu ya tokare ni ," INA SON SHI WALLAHI INA SON SHI," Kalmar ta ta ƙarshe ita ta sa samy baby kwashewa da dariya bayan fitar ta daga ruɗanin da kukan yakakar ya haifar mata shi da farko ,"    Shashashar banza yanzu ke yaks akan soyayya kike wannan uban kukan ? Kamar wacce aka cewa uwar ta ta mace ? To wai ma tsaya yaushe kika fara soyayya ban sani ba ? Duk kuwa da kashedin da nake yi miki ? Koh daga tafiyar da nayi ta sati biyun ce har kananan ƴan iskan nan da nake raba ki da su suka samu damar hure miki kunne ,ah lalle fa ga ki kuwa kin sauya kin yi lumui lumui kin cika kin yi clean , hala saurayin naki mai ɗan gwaɓi-gwaɓi ne naga ya wanke min ke , ah toh ai babu laifi tun da mai maiƙo ne ,"       shi ya baki wannan kuɗaɗen kenan ? ," ta furta hakan tana mai bin kuɗaɗen da kallo , " idanun ta suka sauƙa kan ɗan wani hoton fasfo wanda ga alama daga tsakanin kuɗin ya fito , ta kai hannu gami da ɗaukar hoton ,       Hoton sa ne sanye da kakin sa na soji daga kirjin sa zuwa fuskar sa ," kallon hoton tayi da kyau tabbas ta san shi abokin saurayin ta nuhu ne ,'bata manta ba nuhu ya bata ɗan takaitatcen tarihin sa a wani yammaci da taje bariki wurin nuhu ta tarad da youssouf ɗin , bayan tafiyar sa take tambayar nuhu  yaya ta ga launin uniform ɗin su ya banbanta ? Nan ya shaida mata youssouf sojin niger ne , ya ɗora da bata labarin sa kar ki gan shi haka anan fitattace ne a ƙasar su ɗan sarki ne , yarima ne mai jiran gadon birnin maraɗi ,babbar masarauta ce a niger ,"      Yaks wanene wannan ?? Ko shine masoyin naki ? Da sauri yakaka ta ɗago kan ta domin ta ga wanda samy baby take kira da masoyin ta ,     Idon ta ya sauka akan ƙaramin hoton biyamuradi , da sauri ta kaiwa hoton chafka !      Shine wallahi shine , ina son shi dan Allah anty idan kin san shi , ki kai ni wurin sa ,"    Cikin mamaki samy take yi mata kallon kan ki ɗaya ?    Ke yaks wannan ne saurayin ki ? Kar ki min ƙarya , gaya min ta yaya ya zama saurayin ki ?     Yakaka bata boye mata kome ba daga ranar haɗuwar su ta farko da youssouf zuwa yau ,"        Jinjina kai samy bby tayi bayan ta gama jin bayanin yakaka da ta tabbatar ba ƙarya bane ,! Domin ta san goge yaks a ɗan ƙaramin lokaci ta zama fes yadda ta gan ta sai mai kuɗi , Idan kuwa hakane babu shakka tayi farincikin ƙulluwar alaƙar sa da yakaka , daman irin namijin da take mata hange kenan wanda zasu tatsi arziki daga jikin sa  !tab , ai batun yace ya rabu da yakaka ma zancen iska ne , wasa tsakanin sa da yakaka yanzu aka fara , zata yi duk yadda zata yi taga mu'amalar sa da yaks ta ɗore , har sai ya gama wanke yaks ya zamar da ita mace mai aji yadda baza ta yi wahala ba wurin samun irin sa ko ma wanda ya fi shi koh da shi ya zo ya bar ta , ! Ai da ruwan ciki akan jaa na rijiya ,' idan yaks bata wanku ba ina zata samo masu attajirai irin wanda take buri???       Share hawayen ki yaks idan wannan ne na san shi abokin saurayi na ne , duk inda yake sai na nemo miki shi , kin ji ? Bai isa ba ya wurgar da ke bayan ya morewa ƙuruciyar ki , dole ya zo ya ƙarasa aikin da ya fara ," Cikin murna yakaka ta fara share hawayen ta , tana jin damuwar zuciyar ta fiye da rabi ta kau , jin cewar samy baby ta san bature kam silum har tayi mata alkawarin nemo mata shi ,"    A saboda murna tana tattara ƙudaɗen da ya bata , ta miƙawa samy baby ,"      Ga shi anty na baki gaba ɗaya ! Da murmushi samy baby take kallon ta , sa hannu tayi ta karɓi kudin ta ƙirga su dubu arba'in da shida ne ," Naira dubu goma ta zara a ciki ta miƙawa yakaka sauran ,"     Ki riƙe sauran kuɗin a hannun ki zasu miki amfani kafin na gama shirya yadda zan yi na dawo miki da yarima , wannan wanda na ware kuma , kafin ya dawo ku cigaba da harka dole zamu je asibiti a baki kariya daga samun ciki , kin sai dai ba'a cin moriyar bariki idan ana yi ana kwasar ciki .     Da sauri yakaka ta amince da shawarwarin samy baby , nan dai suka ƴar taɓa hira samy baby tana sake kitsawa yaks shawarwarin yadda zata riƙe yarima idan ya dawo ,     Falmata tayi jugum a zaune tana tunani, wata irin kewa take ji , tun da yakaka ta samu aikin da take yi yanzu  ya zama bata da lokacin ta irin da , duk da cewa dai idan tana gidan tana bata kulawar sosai da sosai bugu da ƙari ga cimaka masu kyau da daɗi da suke samu a yanzu , ga wasu ranakun ma biya yakakar take yi ayi aikin wanke-wanken falmata , amma duk hakan sun gaza samar da farin ciki mai daɗi ga falmata ,yanayin su na farko da ko yaushe suna tare yafi mata kome daɗi , bata da kowa bayan yakaka ,! Ga shi wannan aikin da yakaka ta samu yana neman raba tsakanin su , domin a yanzu duk zata iya ƙirga ƴan awowin da suke yi tare da juna a wuni , daɗewar da yakaka tayi yau bata dawo daga wurin aikin ba ya dagula ran ta , tana aunawa da zafin ranar da yake buso ta tare da kusancin ranar da take ji a jikin ta ta tabbatar yanzu rana ta fara kaiwa tsaka ! Ina yakaka take tun jiya da yamma har yanzu bata dawo ba ? A hankali wasu siraran ƙwallah suka silalo zuwa kan ƙuncin ta ,!   Bata ji zuwan ta wurin ba , sai saukar hannun ta taji ta share mata ƙwallar ,! Cikin ƙaruwar rashin kuzari akan wanda tafiyar youssouf ta jawo mata ganin hawayen falmata ya sake taɓa ranta , " ta zauna daga gefen falmatan        Falmata na ! Meyasa ki kuka ? Wani abun aka miki ? Ko baki da lafiya ne ? Yakaka yanzu kin rage kula da ni , bayan kuma kin san ke kaɗai nake da ita wacce take bani kulawa , " yakaka dan Allah nima ki yadda na dunga bin ki sabon wurin aikin ki nafi son koyaushe muna tare duk inda muke , bamu da kowa sai junan mu ,"    Kiyi hakuri falmata nima daga yau ɗin bazan sake zuwa ba !         Meyasa baza ki je ba ? Ni fa ba nace ki daina zuwa bane , toh shikenan na hakura ki dunga zuwa kin ji ,?    An dakatar da aikin ne wanda nake yiwa aikin ya tafi ,! Sai idan ya sake dawowa watarana ,"    Cikin rashin jin daɗi falmata ta karya wuya ,       Kai amma banji daɗi ba yakaka mutumin yana da kirki , tun da kika fara aiki a gidan su muke samun jin daɗi .,'     Uhum ,!      Cewar yakaka tana mai miƙewa Bari na sauya kaya na nazo kan aiki ,! Chan ƙasan kayan ta a kusa da kuɗaɗen niger da agogon sa da ya bata a haɗuwar su ta farko ta ajiye hoton tare da kuɗin hannun ta , a ran ta tana jin hoton sa da agogon sa zasu zame mata abun ɗebe kewar sa kafin samy baby ta dawo mata da shi kamar yadda ta alƙawarta mata ! Washagarin ranar samy baby ta samu yakaka , suka je asibiti ƙarƙashin jagorar wani nurse abokin hulɗar samy baby , tare da taimakon sa aka yiwa yakaka allurar hana ɗaukar ciki , ba tare da an tsawaita binciken ina mijin ta ba ?, tare da tunasar da ita dawowa sake yin wata allurar duk bayan watanni uku !   Yakaka bata ji ko ɗar ba sai ma farin ciki da take ji chan ƙasan ran ta a domin kan hanyar su ta zuwa asibitin samy baby ke sanar da ita a yau ɗin nan zata garzaya barracks wurin nuhu inda zata samu cikakken bayanin inda youssof yayi bigire idan ma ta kama har inda yake sai ta kai yakaka ! har ɗakin kwanan sa ,! Ah to meye bariki ce fah !  A haka suka tsaya . Sai dai tun dawowar su daga asibitin yakaka ta gaza tsinana wani abun kirki , saboda wani irin murɗawa da marar ta take ta sake , ga duhu-duhu da take gani a idanun ta ,! Gaba ɗaya jin ta take marar lafiya ,' dan haka ta zari nera dubu biyu cikin kuɗin ta ta bawa madam saly tace bata jin daɗi zata je ta kwanta ,"     Jiki na rawa madam saly ta warce dubu biyu tace ta je ta kwanta za'a yi aikin ta .!    Kafin azahar yakaka ta jigata saboda tsabar ciwon ciki da kwankwaso ta takure a guri ɗaya sai murƙususu take  , ! Larki ce ta shigo ɗakin ta tadda ta a galabaice ," nan take tambayar ta meye yake damun ta tace ciki da baya ,'         Cewa tayi ta bada kuɗi a anso mata magani ƙila ciwon cikin al'ada ne daman yana irin haka ,!    Da rarrafe ta jawo jakar kayan ta ta fiddo da duk kayayyakin ta zaƙulo damin kuɗin ta , ta fidda naira dubu ɗaya ta bayar a anso mata magani ,! Ta koma ta kwanta gami da runtse idanun ta !    Da kan ta larki ta je ta amso mata magungunan saboda ta hango moriya , ta kuma ƙulla abunda ta ƙudurta cikin ran ta ," Ta tsaya a wani ɗan shago ta sayo mata ruwan leda guda biyu ! Lamoo ! ta samu yakaka tana sauraran gangar jikin ta ,"    Ta taimaka mata ta zauna tare da ɓalla mata maganin ta miƙa mata ruwan ta kora , ta koma ta kwanta cikin wani sabon yanayin rashin kuzari da take jin kan ta a ciki . Larki ta ɗan saci kallon jakar kayan yakaka , ta gan ta a buɗe yadda ta bar ta bayan ta miƙo mata kuɗin ! Yaks bari na tattara miki kayan naki , ai ba'a bar kayan haka ba ko dan gudun masu dogayen hannu kin san ɗakin namu babu tsaro ,' , Idon ta a rufe ta ɗan gƴaɗa kan ta ,! Da azama larki tayi wa jakar kayan rumfa ta bada baya ga yakaka wacce idanun ta ke rufe ,"      Kayan ta fara mayarwa bayan ta wawuso kusan rabin kuɗin da yake cikin jakar ta chusa a lalitar ta ,"   A ranta tana cewa ! To meye ? Ta san yarinyar sabuwar hannun ce dan haka tana kan ganiyar ta , dan ƴan waɗannan kudaɗen ba kome bane a wurin ta , ƙila ma bata san yawan su ba daga ta shafa ta ji sun ragu , fita zata sake yi wurin masu bata ta sake samo wasu , Dan haka gwara itama ta samu ta wawushe nata , ko ta samu ta kashe wasu matsalolin ta,  ta kuma  farfaɗo da jarin ta na goro da taba ! Da wannan zancen zucin ta kammala maida kayan tsaf ! Ta juyo da kallon ta kan yakaka domin ta sanar da ita ," Sai taga bacci ma take da alama ta samu lafawar ciwon ! Tura jakar tayi inda suke ajiye ta cikin ranta tana ayyana ta samu hujjar da zata kare kan ta ko da ace yaks tayi cigiyar kuɗin ta ," cewa zata yi bata san wanda ya ɗauka ba ita dai ta gyara mata kayan ta fita ,! Sai bayan la'asar yakaka ta farka ! Daga baccin da yake cike da mafarkin biyamuradi da soyayyar sa da ta maƙale mata a zuci !  Watsa ruwa tayi tayo alwala , ta haɗa sallolin azahar da la'asar tayi su , Tsumu tayi a zaune kan ɗankwalin ta da ta shimfiɗa tayi sallah bisa ,  ta rasa abun da ke mata daɗi . Babu laifi taji sauƙin ciwon cikin sai dai sakayau take jin ta ga wani irin ƙuncin zuciya da take ji uwa uba kewa tare da ƙaunar youssouf da take tokarin ta a duk bayan daƙiƙa guda wanda ko da wannan aka bar ta kawai ya isheta cuta ! Ji take kamar ta shekara da barin ganin sa haka ta shafe tsawon daren jiya tana jin kewar sa ta gaza bacci sai juye-juye , Cikin sati biyu kachal da suka yi tare da juna ya mata mugun sabo da soyayyar sa mai tsayawa a zuci , duk da cewa soyayyar ba da baki yake ambato mata ba , a aikace yake idar mata , shiyasa gaba ɗaya take jin kewar sa hatta a fatar jikin ta da kowanne saƙo da lungu na jikin ta ,! Har gizo hannuwan sa ke yi mata a sassan jikin ta ,' ko yaya ta rufe idanun ta fuskar sa take gani tana mata gizo , shi ba ma'abocin murmushi agare ta bane , amma yanayin kamammiyar fuskar sa yana bala'in burge ta , babu shakka a rayuwar ta bata taɓa ganin mutum ɗan gayu mai kyau irin sa ba ! Yunwa take ji domin rabon ta da abinci tun karin safe ," sai dai kallo ɗaya tayi wa robar abincin ta da take ajiye a gefe wanda take da tabbacin wake da shinkafa ne a ciki ta ɗauke kai , ' abinci daddaɗa bakin ta yake kwaɗayi !    Jakar ta ta jawo domin ta ɗauki kuɗi taje sayan abinci wurin su kolo Kallo ɗaya tayi wa kuɗin tasan an taɓa su , da azama ta fiddo su ta ƙirga ta ga dubu goma sha bakwai ne a maimakon dubu talatin da huɗu,! Jujjuya kuɗin take idanun ta sun ciko da ƙwalla , tana da buri akan kuɗin , so tayi ta kai falmata babban asibitin ido a duba ta domin kwana biyu idon yana ɗan matsa mata da ƙaiƙayi kuma suna yin jaa , cikin ran ta bata fidda rai watarana falmata zata gani da idanun ta ba , ji take watarana falmata zata ga hasken da yake wadace cikin sarari duniya , watarana zata ga fuskokin jama'a , zata ga fuskar ta kamar yadda kullum ita take ganin ta ! , sannan idan kuɗin ya rage ta jaa jari ta fara soya doya da kwai da yammaci zuwa dare , kafin dawowar bature kam silum domin ta ɗanɗani daɗin kuɗi da ƴancin da suke samarwa ga mai su ! Baza ta iya sake zama irin na tsananin talauci tare da walaƙancin da ake musu sanadin babu ba !  idan ya so sa dunga raba ribar tare da madam saly , ta san baza ta ƙi ba !, Amma shine wani azzalumin marar imani ya kwashe mata kuɗin ?! Tunanin larki ya faɗo mata arai , ko ita ce ta ɗauka ? Amma larki anya zata ɗauki kuɗin ta ? Koma waye na bar shi da Allah ! Ban yafe ba .    Ta furta hakan a sarari tana share guntuwar ƙwallar ta , ta zari naira dubu ɗaya , a ranta tana tunanin chanjin ta da ya rage hannun larki , bata ,  bata ba ko maganin na dubu ɗaya ɗin ne ? Ita dai baza ta tambaye ta ba idan ma ta cuce ta dan kan ta ! ¿ Kai tsaye ta wuce rumfar su kolo , ta miƙa kuɗin tace a bata tuwon shinkafa da miyar yakuwa , malmala biyu da nama guda huɗu , Kolo ta miƙo mata tuwon a naɗe cikin leda tare da miyar a wani ɗan kwanon roba bayan ta gargaɗe ta akan ta dawo musu da kwanon miyar  ! Kai tsaye wurin wanke wanken falmata ta wuce , ta tadda ta wanke-wanken sun taru tana ta faman wankewa ana ƙaro wasu , saboda yamma tayi lokacin ciniki ne kuma an kusa gama sayarwa ! Alamun gajiya ya bayyana a gare ta ,ga gumi da ta haɗa fiye da rabin zanen ta a jiƙe yake da ruwan wanke-wanken! Ajiye abincin hannun ta tayi a gefe ! Cikin ruwan kumfan ta sa hannu gami da zare soson daga hannun falmatan ,       Kawo nayi sauri na gama , kin ci abinci falmata ?? Da murmushi a fuskar ta ta cire hannun ta a ruwan gami da goge hannun ta a jikin rigar ta ,'     Ban ci ba yakaka , kin ga aikin yayi yawa wanke wanken ina yi ana ƙaro wasu ,"     Amma yanzu zan samu nayi sallah sai na ci ,"     Da ido kawai yakaka ta bita lokacin da ta matsa jikin fanfo ta fara alwala ,"    Ɗan kwalin ta ta shinfiɗa tayi sallar azahar da la'asar akai , bayan ta idar , tace yakaka ta bata abincin ta ,da ta rufe shi da faranti a gefe ,"    sai lokacin yakaka ta lura da yasashiyar robar abincin falmata da take buɗe , ɗaukar robar tayi tana kallon abincin da ana gani an san ƙarshen tukunya ne ƙanzo-ƙanzo ,babu wani mai da yaji na kirki cincirindon ƙudajen da suka tashi daga kan abinci ya sa ba shiri yakaka ta juye shi a bakin makwarari ta wanke robar ta ɗauraye , Ta ɗauko malmalar ɗaya ta sawa falmata ta sake gutsuro rabi ta ƙara mata ta juye mata fiye da rabin miyar , ta kai mata tuwon gaban ta ,' tare da taro mata ruwa a kofi daga bakin fanfo , ita ma ta zauna daga gefe tana cin guntun tuwon ! Suna ƴar taɓa hirar su kamar yadda falmata take so , cikin hirar su take sanar da ita ta shirya gobe zata kai ta ita ma a wanke mata kan ta tare da yi mata kitso ! Bayan sati biyu Rayuwa tayi wa yakaka tsanani wanda ba kome ya jawo hakan ba sai rashin  bature kam silum , domin cikin satin biyun da suka biyo bayan ranar haɗuwar su ta ƙarshe , kamar yadda samy baby ta alƙawarta mata zata nemo mata shi ta wurin abokin sa ,!   Ta je barracks ɗin sai dai bata tarar da shi Colonel nuhu ba, an tabbatar mata da ya tafi bakin aiki ,! Wanda hakan sam bai mata daɗi ba kuma ta kirayi duk numbobin sa basa tafiya ta rasa dalilin haka ! ? Zuwan ta daban-daban uku bata samun sa , dan haka ta ɗan tsahirta .tare da cigaba da lallaɓar yakaka wacce ta lura tayi zurfi cikin mahaukaciyar soyayyar mutumin da a yanzu take hasashen yayi wa yakaka nisa , sai dai a nemo madadin sa ! Wanda bata ga alamun samun haɗin kan yakaka wurin nemo madadin na sa ba ! , babu ranar da yakaka bata kuka akan soyayyar bature kam silum , ɗakin samy baby nan ne wurin fakewar ta ta sha kukan ta domin ita tasan matsalar ta ita tasan dalilin kukan ta , kuma ita take zaton zata iya share mata hawaye , sai dai a yanzu labarin ya sha banban kuma wankin hula na neman kai su dare ,! A yau yakaka ta tashi bata da ko sisi domin satin da ya wuce ta kai falmata asibitin ido da kuɗaɗen hannun ta inda kuɗin magunguna da wasu aune-aune , ya lashe fiye da naira dubu takwas , a cikin sauran dubu goma sha biyu da ƴan kai da suka rage mata , Da sauran kuɗin tayi amfani wurin cigaba da hididimun yau da kullum , musamman abinci wanda shine kan gaba wurin lashe mata ƴan kudaɗen domin kwanan nan ta tsinci kan ta cikin wani irin bala'in kwaɗayi , bata iya cin abincin da bai wadatu da kayayyakin ƙawata girki ba , bata kuma cin abinci babu nama sannan a rana bata sha lemon kwalba "pepsi " ba tasha guda uku safe rana dare ,' idan kuwa bata sha ba babu zaman lafiya wani iri bala'in yunwa mai tafe da tashin hankali zata dunga ji ," Da haka kuɗaɗen hannun ta tas suka ƙare ! Duk da tarin damuwar da take cin ta cikin rai , kallo ɗaya za'a mata a gane ta sauya , ta sake fari har tana ɗaukar ido ta cika tayi luwai-luwai kyaun idanun ta kamar gilashi sun sake haskaka ,! Tana zuwa wuri take ɗaukar hankalin jama'ah . Ture jakar kayan tayi gefe ta ƙarasa bajewa ta zauna daga durƙuson da tayi ta tallafe kumatun ta da hannu, wannan shine karo na uku tana chaje cikin kayan ta a safiyar yau ko Allah zai sa tayi gamdakatar da wani makararren chanji , sai dai koh alamar kuɗi bata gani ba idan aka ɗauke kuɗin sefa ,"niger", wanda basu da wani maraba da babu a wurin ta ," A hankali ta miƙe tana haɗa hanya saboda wata azababbiyar yunwar da take wuji-wuji da ƴaƴan hanjin ta ,' Ɗakin samy baby tayi wa tsinke ,'   Saɓanin zaton da tayi zata tadda ta tana bacci ta jira tashin ta , sai ta tarad da ita tayi shiri tsaf , tana zaune bakin gado tana shirya kayan ta cikin ƴar jaka ta matafiya ! Gaishe ta tayi cikin ladabi ! Yauwa yaks daman yanzu nake son na tura a ƙira min ke , tafiya ta taso min jiya-jiya cikin dare Honourable yake sanar min zamu yi tafiya tare da shi zuwa abuja inda zai je wani aiki watakila ma mu wuce dubai daga chan ," ga waɗanan kayan ki ɗauka na bar miki su , ni nasan a chan zan taho da wasu masu zafi ," ta furta hakan tana mai turawa yakaka wasu kayayyaki da ta ware su gefe,! Yakaka wacce tun da taji kalmar tafiya jikin ta ya sake yin sanyi laƙwas ,! Ta durƙusa bisa guiwar ta ,' a gurin samy baby take ɗan samun nutsuwar zuci , take kuma ɗan taimakon ta da wasu abubuwa ,  baza ta so ba ta tafi ta bar ta a wannan halin tsaka mai wuya da take ciki ,     Cikin sanyin murya tayi mata godiya , bayan ta haɗa kayan ta ƙulle su a ɗankwali ,'     Cigaba tayi da zama tana bin kowanne motsi na samy baby da ido cikin ran ta tana ayyana dama ita ma da bature kam silum ya tashi tafiyar sa ya nemi rakiyar ta mana ? !     Lura da yadda jikin ta yayi sanyi yasa samy baby , ta ce       Ni bani ma lambar wayar ki idan naje ma dunga yin waya , ba kina da waya ba ?     Gyaɗa kai tayi Amma ban san nambar ba wayar ma tana ƙasan kaya na babu chaji ,    Mts idan banda ke yaks waye zai saka waya ƙarƙashin bacco ? To wannan ai ko yariman ma ya kira ki ba sani zaki yi ba ," gidadancin ki yayi yawa yaks bari dai na dawo daga tafiyar nan inaga darasi zan fara baki dalla-dallah    Ƴar takarda ta ɗauka daga jakar ta ta rubuta mata lambar wayar ta ta miƙa mata ,"     Ga lamba ta nan ki kira ni idan kin saka wayar a chaji kuma ki daina ajiye wayar a nesa watakila ma shi baturen naki yayi ta nema bai same ki ba ,'       Cikin ɗan ɓurɓushin farin cikin jin an ambaci sunan masoyin ta tace     Toh anty zan dauko yanzu idan na koma ɗaki , anty kuma yaushe zaki dawo ?     Ban sani ba yaks ni ƴar rakiya ce ! Sai lokacin da ya gam Abun da ya kaushi zamu dawo tare .    Gƴaɗa kai ta sake yi ! Toh anty sai kin dawo Allah ya kiyaye hanya ! ta furta hakan bayan ta miƙe tsaye da ƙullin kayan ta ,"  har ta je bakin kofa ta tsinkayo muryar ta       yaks ungo wannan kƴa ɗan sayi pepsi ki sha tun da yanzu naga yayin ɗaga ƙwalbar pepsi kike ! Ta ƙarasa zancen da ƴar dariya Dubu biyu ta bata , da murnar ta ta ƙarba ," tana jero godiya      Zuwa tayi ta kai kayan da ta bata ɗaki ta dawo domin yi mata rakiya, Tare suka jera yakaka ta ɗaukar mata jakar kayan nata , suna tafe tana sake karfafawa yakaka guiwa ganin yadda duk ta bi ta damu da tafiyar da zata yi , har zuwa bakin babban titi inda ta samu "mai adai-daita ", ta shiga tare da yin bankwana da yakaka ! Akan hanyar ta ta komawa gida tayi zurfi cikin tunanin ƴar ƙanƙanuwar duniyar ta ,wacce babu kome cikin ta sai tarin ƙalubale , mutanen duniya tausayi yayi ƙaranci a zuciyar su , son kan su tare da son dukiya sun makantar da su wurin duban na ƙarƙashin su da ƙyautayi da kyautatawa , kaɗai suna duban na ƙasa da su ne idan wata buƙata tasu ta tashi wanda suke buƙatar wannan ya kawar musu da ita , Da ƙarewar kuɗin hannun ta da tsayuwar rayuwar yancin da ta fara dai-dai suka zo domin tun lokacin da madam saly ta fahimci fa yanzu ta koma faƙiriyar ta kuma ta daina ganin gilmawar mutumin da ya tsaya mata tare da jin yayyafin nerar da yake yi mata , ita ma taci burki daga duk wani mutunci da lallaɓawar da take yiwa yaks , ta koma karta mata walakanci tare da bautar da ita ," ah toh me zata jira ? Ai kawai ungulu ta koma gidan ta na tsamiya , jaki ya tai gidan uban sa ! Ita ba gallazawar bautar aikin yafi damun ta ba illa yadda ƙarfi da yaji madam saly ta fara kai ta gaban ƴan iska tana tallar ta , ita baza ta jure hakan ba , bayan bature kam silum bata jin zata iya yadda da wani ɗa namiji har suyi abun da suke yi tare da shi ,  cikin su wanene mai kamannin sa ? Mai tsaftar sa ? Mai wayewar sa ? Mai gayun sa ? Mai irin ƙamshin sa ? Babu ! Idan kuwa haka ne ita baza ta yadda da kowanne ƙaton ɗan iska ba bata son su ! Zata jure kowanne irin aikin bauta da wahala , amma ban da harkar taimako ta wannan sigar , bature kam silum kaɗai yake da wannan ƙimar a gurin ta , zata zauna zaman jiran sa har ranar da zai dawo gare ta ! Da wannan tunanin ta ƙaraso shagon "fashe mai shayi ! Tace a fasa mata ƙwayaye shidda a soya su da indomi manya biyu , a haɗa mata shayi da madarar ɗari bonbita na hansin ! Ta miƙa kuɗin aka bata ƴan chanjin ta . Aka sarrafa mata aka zuba a leda ta ƙarba , Shagon gefen sa ta wuce ta sayi lemon kwalba na pepsi mai sanyi , Ran ta ƙwal ta dawo cikin gidan kai tsaye ta wuce cikin ɗakin su falmata , a zaune ta tarar da ita , ta ajiye kayan hannun ta gami da ficewa taje ta wanko kofuna biyu da faranti ɗaya ta zo ta juye musu ,       Falmata matso muci! Lomar yakaka ta ɗaya ta biyu ta zare hannun ta daga cikin abincin sakamakon ji da tayi zuciyar ta ta wani hautsina ta yamutsa kamar zata fito ta baki , nan take tsinkakken miyau ya taru a bakin ta ," ta matsa gefe tana jan numfashi . Jikin ta har rawa yake ta balle murfin pepsi da haƙorin ta ta kafa kai tana kwankwaɗa , ba dire ba sai da ta shanye ," Sai dai me wani irin ƙugi da cikin ta yayi falmata da kan ta ta jiyo , kafin ta ankara wani kakkarfan amai ya taho mata , nan ta dunga kwarara shi a ɗakin daga bakin kofa , kaf abincin da ta ci tun daga na jiya da dare da bai kai ga narkewa ba har zuwa ƴar indomi ɗin yanzu sai da ta amayo su , amai har ta hanci , ga hawaye da yake ta tsiyaya a idanun ta , yunƙurin aman ta har kofar rumfar su ana jiyo sautin sa ,' har ta koma sai kakaru bata amayo komai sai koren yawu ," Falmata ta gigice da ya sa ta fatali da kofunan shayin nasu tare da bi ta cikin farantin indomi ta ɓarar da sauran , cewa take    Yakaka yakaka yakaka , meye ya same ki ? Meye ne ? Baki da lafiya ne daman ? Me kika ci kike amai ? Da lalube ta ruƙo yakakar zuwa jikin ta bayan tayi zaune dirshan cikin aman da yakakar tayi ,     Rashin amsa mata da yakaka tayi wacce take ta yunkurin amai har muryar ta ta shige ciki ya sa falmata fashewa da kuka tare da fara kwala ƙiran neman agaji ,' ihu take tana neman taimako     Daga bakin maƙwarari inda hema da larki suke wankin dawa suna jin su duk yunƙurin aman da yakaka take sun ji sarai sun kuma riga sun yi hasashen abun da ka iya sanya ta aman dan haka suka yi biris , ! Yo ina ruwan su ? Sun ga ire iren ta yafi sau shurin masaƙi , '     Rabu da shegiyar yarinya , ba dai ita tace bariki zata yi wa shigar sojan badaskare ba ? Sama ta ka ba tare da ta ɗau darasi ba , ai kuwa zata ɗanɗani kuɗar ta , wannan somin taɓi ne daga cikin illolin faɗawa bariki ba tare da an nemi ilmin sa ba ," cewar hema     ihun da ya yawaita ya farkar da madam saly daga baccin tofon girar da take shaƙa a gigice ta bazamo kan ta babu ko ɗan kwali guiguyayyar ƙeyar ta da sanƙon ta sai ɗaukar ido suke a hasken ranar da ta fara ɗagowa , " cewa take        Wace masifar ce ta faru da farar safiyar ne ? Waye ya mutu ? Waye ya sha azaba ? Ake faman kururuwa haka ?    Kai tsaye ta nufi ɗakin su hema inda take jiyo tashin ihun falmata ," Turus ta jaa ta tsaya ," yawata idanun ta tayi cikin ɗakin tana ƙanƙan da ido kafin ta lailayo wata ƙazamtatciyar ashariya ta watso ," ta ɗora da         Na shiga uku na lalace ni salaha dan uban uban ku yakS me nake gani haka ? Gasar amai kuke koh me ?wace iriyar shegiyar ƙazamta ce wannan irin taku ta ƴaƴan ƙauye kuke gwada min haka a cikin gida ? Tab toh da sakel wallahi baza ku korar min kostomomi ba , yo wannan ai idan ɗaya daga cikin kostomomi na suka ga wannan iskancin ƙazantar da kuke babu ni babu ƙara ganin wani ya zo sayan ruwa ," dan babu mai yadda ya ci abun da kazamtattu irin ku suka taɓa ,!     Wata irin damuƙa tayi wa kafaɗar yakaka ba tare da ta kula da halin galabaita da take ciki ba , ta hankaɗo su waje tare da falmata wacce ta maƙalƙale jikin yakakar ," suka tafi suka faɗi tare nan yakaka ta ƙarasa bajewa a ƙasa cikin halin rashin sanin inda take , Shegiya tsinanna yo wani ɗan iskan ya aike ki kije ki maƙalo ɗan tayi a mahaifar ki ? Ai ni daman kallon ki kawai nake ina jiran ranar da cikin zai baiyana kan sa , ko ta arziƙi ko ta tsiya , amma tun tuni na farga da shi  , shegiya marar sa'a daga fara bariki har kin ɗauko ciki , to kar ki ji da wai ni bana rainon  ƴaƴan shegu a cikin gidana dan haka ku san inda dare yayi muku , arziƙi nake nema ba tsiya ba baza ki raɓe ni da shegen abun da yake cikin ki ku maƙalamin asara da rashin sa'a ba ," yo ƴaƴan halas ɗin ma wasun su amfanin me suke tsinanawa kan su da iyayen su idan ban da masifa ? Haure kafafun yakakar tayi , idan kin gama watangaririyar ki a ƙasa sai ki tashi ku hau shiri , ban ji zan iya ba rainon ɗan shege ! ki bar ni naji da kaina ! Wani irin bugu zuciyar falmata take da kalaman madam saly suke sauƙa a kunnuwan ta , wai me take cewa ?waye yake da cikin shege ? Ɗan shege waye zai haife shi ? ta san ɗan shege sarai domin kuwa akwai wata ƴar makotan su da ta taɓa yi , iyayen ta suka kore ta , kowa a unguwar su ya tsane ta , jama'ah suka ta yin Allah wadarai da ita ,  mamar ta ta dunga kuka har ta daina fita layi , bata san ma'anar cikin shegen ba sai da ranar ta nacewa maman su da tambayar ma'anar kalmar,"a taƙaice ta bata amsa haihuwar yaro ba tare da anyi aure ba shine cikin shege," har garin su ya watse ba'a san inda wannan yarinyar take ba , tabbas cikin shege abu ne marar kyau matuƙa , madam saly tana nufin irin shi yakaka tayi ? Tunanin ta ya katse lokacin da ta ji yakaka ta jaa wani numfashi tare da sake yin wani yunƙurin aman  ,"     Wani sabon ihu ta sake saki ,"    Dan Allah ku taimaka min kar yaya ta ta mutu dan Allah ku taimaka mana ," yakaka ki min magana dan Allah ki daina shiru , ki tashi yakaka ki tashi ,      Larki ce ta bar abun da take gami da nufar bakin fanfo ta taro ruwa a wani kwanon silver gami da sanya wani bokitin a bakin fanfon , a kaikaice ta ɗago yakaka wacce take ta sakin numfashi'ita ba sumammiya ba ita kuma bata motsin kirki ," ta kafa mata kwanan a baki ,      Bata wani shaa na kirki ba ta cigaba da yunƙurin aman,"     Aifa lalle kin gamu da wahala , gwara ma idan zaki tashi ki ta shi domin a gidan nan babu wanda zai damu ko mutuwa zaki yi a nan a yashe sai dai a tsallake ki a wuce ,  masu mutuncin ciki sune zasu jaa ki gefe a samo mai miki salla a je a turbuɗe ki , dan haka ma gwara ki bar lamɓo ciki ba kan ki aka fara ba , laulayi kuma dole ne tun da har kika iya zuwa kika kai kan ki aka maƙala miki maƙalalliya, kin dai ji abun da ,"saly fara," tace ki fara shirin bar mata gida ,"      Juye mata ruwan bokitin da ta ɗauko tayi akan ta baki ɗaya ta jiƙa su sharkaf har da falmata wacce take ƙwaƙume da yakakar , daga ita har yakaka ba sauraran bayanin bakin larki suke ba ," wacce ita ce ɗaya da ta kula su , ta zo kan su duk da cikin walakanci take musu Abun da ita a wurin ta taimako ne !    Nan ta dangwarar da bokitin gefen su ta wuce bakin aikin ta tana cewa ,"     Sai ke kuma ki tashi ki je ki wanke ɗakin da kuka gama chaƙuɗa shi da kazantar , sakarkarun yara ƙyauyawa ! Sanyin ruwan ya taimaka wurin farfaɗo da yakaka daga halin gigitar da ta shiga ," da taimakon falmata ta miƙe zaune ," yadda kan ta yake juyawa tare da wani irin bala'in ciwo ya sa ta kama kan nata da hannu biyu,"   Falmata kaina zai fashe ,'! Sannu yakaka ki tashi na kai ki ɗaki ki kwanta ,'   A wajen kwanciyar  ta,  ta taimakawa yakaka ta kwanta , fita tayi ta lalubi bokitin da larki ta ajiye ta ɗauka taje ta taro ruwa a cikin sa ta komo ɗakin ,"ita bata san inda tsintsiya yake ba a gidan , dan haka ta laluba ta tattara kofunan da farantin ta haɗa su wuri ɗaya , kasancewar ɗakin daman Ledar sa ta riga ta ratattake ta zama gutsirarra ,ta wurin da suke kwanciyar , daga tsakiyar sa zuwa bakin kofar dandaryar siminti ne , sai kawai ta kwarar da ruwan ta wuraren da take jin lema-lema , ta sa takalman ta biyu ta kwarfe ruwan ta tura shi wajen kofar ,' Duk abun da take yakaka wacce idanun ta suke lumshe tana jin ta , karfin tashin ne bata da shi , wata iriyar mummunar kasala take ji tana bin duk gabobin jikin ta , ga juyawa da kan ta yake yi ɗakin kan sa juya mata yake ," Gefen yakaka ta dawo ta zauna , cikin ran ta tana fatan lafiya ga yakakar wacce take zaton bacci take ," Ko mintoci biyu basu ƙarasa ba suka ji muryar madam saly tana ɗuro musu ashar ,"     Ni za'a kawo wa iskanci da tsaurin ido , dan uban ku ni da gidana ina cewa ku fita kuna yin biris da ni , sai kace da uwar ku muka haɗa kuɗin sayan gidan ?? To billahi minti goma yayi kaɗan zan sa a fitar min da ku bayan an chasa min ku ," yau naji jaraba da maSifa ,"   Tana gama hanya ta fito ta durƙusa a gaban madam saly gami da fashewa da kuka ,"     Madam dan Allah wanne laifi na miki zaki kore mu ? Ke kaɗai ce gatan mu dan Allah ki yafe min laifin da nayi miki , idan mun bar nan bamu da wurin zuwa ,"! Ji min mayyar yarinya ? Ta ina na zama gatan ku ? Babu dangin iya babu na baba ? Na gaya miki yaks ni bana jurar asara , asara ce babba na ci da ke na ci da ɗan cikin ki ? Yo wanne aiki kike min da har ya kai na dunga ci da rai uku a biyan aikin ? Ga ki ga ƙanwar ki kuma ga ƙarin wani yanzu kin maƙalo a cikin ki ,' idan har kina son zaman gidan nan sai dai ki samo uban cikin jikin ki nayi masa lissafi kuɗin abincin ɗan sa ya lale ƙuɗi na ya biya ni sannan ,! Tab ina zan iya asara ? Ɗa a cikin ta ? Wacce magana ce wannan madam saly take faɗi ? Ko dai kunnuwan ta sun daina ji daidai?    Madam wane ɗa ? Ina ɗan yake ? Yana ƙundun uwas ki yaks nace yana ƙundun uwas ki , ni zaki yiwa bariki ? Ah lalle fa gwada min firirita irin ta sabuwar karuwa ," Sunkui da kai yakaka tayi kan ta yana sake ƙullewa ," Wai zaki ki kira ɗan iskan da ya ɗirka miki cikin  ya zo ne ko kuwa kin zaɓi barin gidan ?     Da sauri tace ! Zan kira shi madam   Na baki nan zuwa gobe duk inda ɗan iskan yake ki nemo shi yazo ya biya kuɗin ci da ɗan tayin sa ko kuwa yasan inda zai yi da ke ,!  Madam saly ta furta hakan tana mai wucewa ta bar wurin cikin ran ta kuwa tana ayyana irin kuɗin da zata iya samu akan cikin jikin yaks domin kuwa ta san da mutum ɗaya tak yaks tayi harka , bata shakkun shi ya fara sanin yaks kuma shine uban cikin jikin ta , idan kuwa haka ne ai ita ranta ƙwal , tun da ta lura da samuwar cikin take farin ciki tare da ƙulla yadda zata yi wannan ciki ya buɗe mata sabuwar hanyar kama kuɗi a hannun wannan hamshaƙin attajirin da yayi mata ɓarin naira akan taraiyar sa da yaks , wanda bata tantama wani hamshaƙin attajiri ne mai muƙami , ko kuwa dai ɗan attajiran , da har yau take mamakin ina baƙauyiya kamar yaks ta samo shi ,?  shi kuma cikin jerin gogaggun matan duniya da suka dace da shi ya rasa ta zaɓa sai ya tsallako kan yaks ? Kai ita tafi danganta tarayyar sa da yaks ma da neman wani cikar burin sa na daban , wata ƙila sa'a aka bashi aka ce ya haɗa da neman kuchakar mace irin yakaka ,wata ƙila kuma wani al'amari ne mai girma ya jirkita tunanin sa da har ta kai shi ga neman yakaka , ita dai ta san ruwa bai tsami banza ! Koma meye ita gaba ta kaita !    Harƙƴalla da irin su babbar sa'a ce . Ko batun korar da tayi wa su yakakar , barazana ce kawai ta shirya mata domin ta zaburar ta ta nemo mutumin da ta lura a yanzu bai cikin rayuwar yakakar , da ita kuma take ganin rashin sa a matsayin wani babbar asara , dole ya dawo ya cigaba da harka da yaks ita kuma ta cigaba da samun maƙudan kuɗaɗe ta sanadin hakan ,! Ta shafe fiye da mintoci biyar a durƙushe nan wurin tana tunani , sai dai duk yadda ta kai ga son fahimtar inda maganganun madam saly suka dosa ta gaza ganewa ,"     Wanne irin ciki ? Ta san ciki ake a haifi ɗan mutum , to amma ita bata da wani sani akan yadda ake a ɗau cikin ɗan mutum ! Tasan dai sai anyi aure ake haihuwar , to ai ita bata yi auren ba ! Kuma da madam saly take cewa tana da ciki , ina cikin a jikin ta ? Cewa take cikin mata huruwa yake ya zama ƙatoto sai a haihu ,? Ita kuwa nata cikin shafal yake ,"babu ko alamun tudu ," Wata sabuwar tambayar ce ta kutso cikin tunanin ta , toh kuma waye baban ɗan cikin nata da madam.saly take cewa ta nemo ?   "Bature kam silum" wani sashi na ran ta ya ayyano mata sunan sa a matsayin uban ɗan cikin ta da ake ikirarin tana da shi ,"     Ɗan wani tattausan murmushi ya ratso tsakanin hawayen fuskar ta ya bayyana kan sa ,"        Kome da ya dangance shi sanyata nishaɗi yake tare da farin ciki duk kuwa yadda ta kai ga shiga halin damuwa da tashin hankali ƙaunar sa daban ce cikin ran ta tafe take da wani irin kakkarfan shauƙi mai bata kuzari ,'        Ina son ka dayawa ! ta furta hakan a sarari tana mai dafe marar ta da take ɗan yin ciwo kaɗan ,"     Karaf kalmar ta sauka a kunnuwan falmata wacce jin wucewar madam.saly da yadda ta kaya tsakanin su da yakaka , ya sanya ta fitowa duba yakakar bayan ɗan gajeran zaman jiran shigowar ta ɗakin da tayi domin akwai tarin tambayoyin da take son yi mata ," Rashin shigowar yakaka da wuri ya sanya ta gaza jiran ta , sashin ran ta na fatan ba ciwo ne ya sake turnuƙe yakakar ba , sai dai kalmar da taji yakakar ta ambata a kunnuwan ta ya sanya ta sa kalmar a jerin tambayoyin da take son yi mata . Hannu ta kai ta lalubo kafadun yakaka ta ɗora hannuwan ta duk biyu kan kafadun tana fuskantar ta ta buɗe idanun ta sosai tamkar dai tana Ganin ta ,     Yakaka dagaske ne kina da cikin shege ? Zaki haifi yaro ba tare da kin yi aure ba irin na falta?     A hankali ta sauke hannun falmata daga kafaɗun ta , ta rike hannayen cikin hannun ta ," tare da yin ƙasa ƙasa da muryar ta ,"    Bani da cikin shege falmata ƙarya madam take min so kawai take ta kore mu ,!     Ɗan jim falmata tayi cikin rashin gamsuwa ,! Kafin ta sake jefawa yakaka wata tambayar     To waye ne naji kin ce kina son shi dayawa ? Waye shi ?     Kallon fuskar falmatan tayi a ɗan hargitse tana jin wani yanayi cikin ran ta ,"        Bature kam silum ! ,"yakaka ta furta hakan a ƙasan maƙoshi.    Ɗan zaro idanu falmata tayi tamkar tana ganin ta ," Nduwodo bature kam silum ? Ndan shaa noum3 ? ( wanene bature kam silum aina kika san shi )    Kaam shaa banaangndi3 .' ( mutumin da na taimakawa ) Chaaman shaa ra'amaa ? ( daman son shi kike ? ) Shii shaawa shaa rumiind3 tayd3zin zayyrod3 , ( yana da kyau baki gan shi ba ɗan gayu da shi ) Ɗan murmushi ne ya subucewa falmata wanda ya zarce zuwa dariya , cikin muryar dariyar ta ce     Har naji ya burge ni NIMA INA SON SHI!      Da wani irin yanayi mai daɗi yakaka ta jaa falmata cikin jikin ta tana jin yadda ƙaunar falmatan yake zagaya duk hanyoyin jinin ta , tun da daɗewa ta sani falmata mai taya ta son abun da take so ne kome lalacewar wannan abun shi yasa ƙaunar falmata ta fifita akan duk wata ƙauna da take zagaye jinin jikin ta !       Cikin satin ta ɗan samu sauƙin walakanci tare da bautawar da madam saly take yi mata saboda kullum cikin gilla mata ƙarya take akan uban cikin jikin ta yana nan tafe , wanda har yanzu ba wai ta yadda da cewa tana da cikin bane , neman hanyar da zata sa madam saly ta haƙura ta ƙƴale ta ta cigaba da zama gidan ta take ,  duk da cewa a halin yanzu duk ta yadda ta ci abu mai ƙarni ko yaya ne sai tayi aman sa wanda yake wahalshe ta sosai , sai kuma a wasu lokutan yawu ya kan ɗan taru mata a baki ,  bayan hakan babu wani alamun ciki da ya bayyana a gare ta wanda ita a ƙaramin sanin ta zai sa ta yadda tana da cikin ,"       Amma ba'a je ko ina ba madam saly ta farga da cewa ƙarya ce yakaka take gilla mata sumfiri-sumfiri wanda hakan ya fusata ta , ta shiga saukewa yakaka kwandunan bala'i da masifa gami da sanya ta aiki babu dare ba rana tana kuma sake tisa mata a kullum cewa gaf take da ta kore su , Daga yakaka har falmata hankulan su a tashe yake akan tsangwamar da madam saly take yi musu , ita yakaka bata san wata hanya da zata bi ta nemo youssouf ba baya ga lambar wayar sa wacce ita kuma tun kwanaki biyar da suka wuce da madam saly ta turke ta ta sa ta kira lambar sa ƙwaya ɗaya jal da yake kiran ta da ita a lokacin da suke tare , sai dai kiran farko da tayi da ya shiga , har ta gama ƙara ba'a ɗauka ba , to tun daga sannan ko ta kira lambar bata tafiya , daga tayi alamun ta shiga sai ta katse , ga alama an datse hanyar shigar kiran daga computer. Gaba ɗaya sun fara lalacewa kasantuwar su duk biyun ba ma'abota son tashin hankali bane daɗi da ƙarin tsoron madam saly da suke yi kamar me ,! Allah Allah yakaka take yi samy baby ta dawo , ko zata ɗan samu sa'ida da wurin fakewa , bakin cikin ta ɗaya akan bacewar ƴar takaddar da samy baby ta zana mata lambar wayar rta bisa ,ta nemi ƴar takaddar ta rasa sama ko ƙasa babu , tafi zaton a tun ranar da ta bata ta yar ba tare da sani ba , a haka kwanaki suka tura , zuwa lokacin da lamura suka fara tsananta gare su , laulayi tuƙuru ya sako yakaka a gaba , kome ta ci amai take ,bata da abun so da kuma yake ƙwantar mata da hankali irin ƙamshin turaren youssouf da yake manne da jikin kuɗin sa na Niger da kuma agogon sa,  duk dare da su take ƙwaƙume cikin zanen rufuwar ta , idan ba haka ba babu ita ba bacci , ɗan ƙaramin hoton fuskar sa ya zamar mata abu ɗebe kewa a duk lokacin da ta ji son sa ya mintsine ta ! ga aikin da madam saly ta walle ta ce bata janyen shi daga kan ta a wai domin tana laulayin shegen cikin ta , a cewar ta ma ita ake ƙwara , kullum cikin zagi da aibata yakaka take da munanan kalamai iri-iri a duk lokacin da taji tana amai ," A halin yanzu duk wani mai shigowa cikin gidan ya san yakaka tayi ciki , ciki kuwa har da ƙawar ta da suka zo gari tare yagana , wacce tun daga lokacin da ta ji da kunnen ta yakaka tana da cikin shege , ta janye mata , magana ta kirki bata haɗa su , haka yakakar zata yi ta bin ta tana so ta bata dama suyi magana amma fir yagana ta juya mata baya taƙi kula ta , ɓaro-ɓaro take nuna ita fa kƴamar ta take yi , da har ta kai a wani yammaci ta gaggasawa yakakar magana ta kuma nemi da ta fice a harkar ta ita ba karuwa bace mai abun kunya irin ta ,"    a ranar kusan raba dare yakaka tayi tana kuka a cikin zanin rufuwar ta bisa teburin kwanan ta , ji take gaba ɗaya ta muzanta domin a zuwa yanzu ta fara amincewa da tana ɗauke da cikin shege a jikin ta ," Sannu sannu rayuwa tayi wahala da tsanani ga yakaka da falmata , domin kuwa a halin yanzu haka suke wuni jibge a gefen ɗakunan gidan cikin yunwa da ƙishirwa , saboda yakaka bata iya yin aikin dalilin rashin lafiya , amai da take ta faman yi ya ƙarar da ruwan jikin ta ga kuma ba abincin kirki wanda hakan ya sa gaba ɗaya jikin ta ya shika yayi yaushi idanun ta har kore-kore suke , babu mai kula ta sai ƙanwar ta wacce ita ma yawan tashi ta zo wurin yakaka idan taji tana amai ko kuma idan tana buƙatar ruwan da take shan sa take dawo da shi , ko kuma ta kawo mata abincin ta da ba iya ci take ba , wannan zirga-zirgar da take yi ya jaa madam saly tace ta dakatar da ita daga yi mata wanke wanken da take yi a cewar ta baza ta yadda falmata ta dunga gwamutsa mata aikin wanke wanke da wankin amai ba ," ta maye guraben su da wasu fallallun ƴan mata biyu , a cewar ta tun da sun zame mata ƙarfan ƙafa , baza su bar gidan ba to su nemi abincin su wurin kwana kuwa su tsaya daga tsakar gidan zuwa cikin rumfa ," Da hakan suka amince domin kuwa basu da wata mafaka bayan nan ɗin yini suke bin inuwar gaban ɗakuna da baccon kayan su da shi ma aka wurgo musu abun su kan su ,  babu mai lura da su , sai idan falmata taji yunwa na neman galabaitar da su ta daidaici lokacin kammala cin abinci ta lallaɓa zuwa bakin  makwarari inda take ɗan tattaro musu guntattakin abinci da ƙanzo-ƙanzo da a yawan lokuta ita ɗaya take ci domin yakaka ko son kallon abincin bata yi bare ta kai ga ci ," Idan dare yayi kuma su koma cikin rumfa su kwana bisa tebura. Falmata ta so ta fara fita bara sai dai rashin ɗan jagora ya hana ta , tayi yunƙurin neman taimakon yagana akan ta dunga kai ta bakin hanya wurin barar ta amma sai yakaka ta hana ta yiwa yaganar magana ," a cikin wannan halin na tsanani suka shafe fiye da sati uku suna watangaririya cikin rashin galihu , tare da yunwa da kirshirwa ,  kwatsam rana ɗaya sai ga samy baby ta dawo bayan ta shafe kusan watanni biyu da ƴan kai bata nan ,  nan ta tarar da yakaka cikin mummunan yanayin mutu Kwakwai rai kwakwai , ba shiri ta kwashe su zuwa wani ɗan jeka na yi kan asibiti mai zaman kan sa ," Nan aka shiga bata taimakon gaggawa , har jini aka ƙara mata leda ɗaya bayan ruwa da tarin allurai da ta sha , Ba ƙaramin faɗa likitan yayi ba da yadda aka bar yarinya ƙarama da ciki jikin ta cikin irin wannan mummunan yanayi , har ma ya nemi da ya ga mijin ta domin su gargaɗe shi     sororo samy baby tayi tana kallon likitan , kafin ta buɗe baki tace     ciki fa likita ? Waye ke da cikin ? Ita marar lafiyar da kika kawo/ƙanwar ta ki   kina nufin baki san tana ɗauke da ciki ba har na tsawon sati goma sha biyar da kwanaki shidda ? ?    Goge gumin da ya tsatsafo mata a goshi tayi ,"     Ban sani ba likita kasan bama tare jiya na dawo daga tafiƴa , ta furta hakan cikin rashim sanin takamaimai amsar bayarwa , cikin sanyin jiki ta miƙe ta fito daga ofishin likitan bayan ya sake jaddada mata lalle ta nemo mijin yakaka ! wai yaks ke da cikin??har na tsawon watanni kusan huɗu , wannan wanne irin ɓata wasa ne yaks take son yi masu ? Ita da ta je abuja ta ga yadda alhazan birni ke rububin ƙananun ƴan mata irin yaks , har tayi mata sha'awar samun irin wannan damar ta dawo da niyyar ta sake wanke ta ta shigar da ita  aJi na musamman ta samu ilmin bariki yadda zata ci ribar sa  su wuce abuja tare ," ta huce takaicin duniya ", hatta waɗanda suka raɓe ta ma su huta , amma shi ne dan rashin sa"a zata zauna da ciki a jikin ta har tsawon wannan lokacin , waye ya gaya mata ana haɗa harkar bariki da jego da rainon ƴaƴa ? Ya zama dole a fidda cikin nan muddin tana so tafiyar ta tayi kyau ! BAYAN SATI ƊAYA . Jikin yakaka yayi kyau ta murmure babu laifi duk da cewa shi laulayi bashi da wani magani takamaimai amma dai ta samu farfaɗowa daga halin galabaitar da ta shiga , sai ɗan abun da ba'a rasa ba na daga larurar masu ɗauke da ƙaramin ciki , kamar kasala , tashin zuciya , yawu da sauran su . dan haka yau likitan ke sallamar ta bayan ya kafa mata dokokin kula da kan ta da lafiyar jaririn cikin ta , ya kuma sake jaddada mata da ta fara zuwa awu cikin wata mai kamawa ," Yakaka wacce zuwa yanzu ta amince tabbas tana ɗauke da ciki a jikin ta domin kuwa ga cikin ya ɗan fara tasowa kuma kaɗan kaɗan tana ɗan jin taurin sa yana dunƙulewa guri guda ,"    Cikin ladabi ta amsawa likitan tare da sake jero kalaman godiya tana mai satar kallon samy baby wacce tayi kicin-kicin da fuska ta ɗauke kai ,"     Cikin da za'a a markaɗe shi shine har ake jero ka'idojin kula da shi ? Ai suna komawa gida gobe zasu shirya ta kai yakaka a fidda mata wannan alaƙaƙai ɗin , abun da ma yasa bata fitar da nufin ta anan ba saboda ana iya chafke su idan aka ji nufin su ," Kai tsaye ɗakin samy baby suka wuce , bayan isar su gida , nan ta shige banɗaki domin watsa ruwa ta bar su a raƙube daga bakin kofar ɗakin , sun yi shiru basa cewa juna ƙala kowacce tana saurarar zuciyar ta , fargabar su ɗaya hukuncin da itama samy baby zata iya aiwatarwa akan su . Ko ita ma korar ta su zata yi kamar madam saly ? Bayan ta gama wankan ta , ta shafa mai ta shirya ta zo ta zauna ta tisa su a gaba ,      Falmata ɗan bamu waje zan yi magana da yayar ki ,"   Toh anty , da lalube ta ƙarasa ficewa daga ɗakin ta fice chan farfajiyar gidan ta tsugunna daga jikin bango . Yakaka ashe har rashin wayon ki ya kai ki zauna da ciki tsawon wannan lokacin a jikin ki ba tare da kin ɗau matakin rabuwa da shi ba ? Kin kuwa san barazanar hakan ga rayuwar ki cikin wannan halin da kuke ciki ke da ƴar uwar ki ? Anty kiyi hakuri nima ban san yaya zan yi ba ,"  ta furta hakan tana me share ƙwallar da ta silalo bisa kumatun ta ," To wai ma ba na kai ki an miki allurar hana ɗaukar ciki ba ? Kin kaini anty , kiyi hakuri ! Mts kome dai aka yi da jaki sai ya ci kara ,!    yanzu sai ki shirya gobe mu je a fidda cikin nan daga jikin ki ,"dan bazai yiwu ki zauna tare da shi ba Ɗas Ɗas Ɗas  zuciyar ta ta buga ,"    A jirkice ta ɗago kan ta dake sunkuye ta dubi samy baby da raunanan idanun ta cikin sanyin murya tace    A kai shi ina anty ? Galala samy baby ta dube ta    a kai shi ina kike tambaya ta ? a subda shi a kwata ya bi makwarari toh meye amfanin sa ? Shiru tayi tana jin yadda zuciyar ta take faman bugu da wani irin tsananin tsoro da ya kama ta makamanci da na mutumin da ake shirin raba sa da gudan jinin sa . wannan cikin bashi da wani amfani a wurin ki illa ya jefa ki a wahala tare da ƙuncin rayuwa , kin dai ga kaɗan ɗin sa yadda ta faru da ku a wajen madam saly , to wannan kaɗan ne akan irin wahalar da zaki iya faɗawa muddin kika cigaba da barin cikin nan a jikin ki , ranar babbar nadamar ki da shiga tashin hankalin ki kuwa shine ranar da abun da yake cikin nan naki zai fito duniya ,toh kiyi yaya da shi ? Ki kai shi ina ? Ki raine shi da me ? Ki kula da rayuwar sa da me ? Idan ya girma ya tambayi ina uban sa ki ce da shi me ?  Amsar ita ce babu ! ke da kan ki yaks kina buƙatar matallafi wanda zai ɗago ki ki tsaya da kafafun ki kema ki taimaki ƴar uwar ki miskiniya , ki tuna baku da kowa baku da kome baku da wurin zuwa baku san kowa ba , kowan ku sun ƙare ,"   mts ta jaa tsaki ni bata lokaci na Ma nake a wofi , ke da na zauna ina faɗawa waɗannan kalaman kin fini masaniya akan su saboda kai tsaye ke suka shafa ,'     Abu na karshe da ni zan faɗa miki shine idan har kika amince muka je aka raba ki da cikin nan ni kuma na miki alƙawarin zan tsaya miki ki shiga harkar bariki da karfin ki , ki ɗaukaka ki tumbatsa ,ki kai gaci , domin garin abuja zamu wuce kina gama warwarewa , idan kuwa har kika nuna ƙin amincewa kamar yadda na hango alamun hakan akan fuskar ki , to ni na janye hannu na akan lamarin ki , ki nemi wurin da zaki baiwa kan ki tare da cikin jikin ki zuwa kan ƙanwar ki mafaka , ni da kike gani ma bazan wuce sati mai zuwa ba zan sake barin gari , ban kuma san ranar dawowa ta ba ," dan haka zaɓi ya rage gare ki yaks ,! Kiyi tunani daga yanzu zuwa gobe     Daga haka ta ɓalle jakar ta ta fidda naira dubu biyu ta miƙawa yakaka ,'    ni zan fita ga wannan ku ci abincin rana da dare ke da ƙanwar ki , ni sai gobe zan dawo , ku kula min da ɗaki na akwai muhimman kaya na a ciki ,! Daga haka ta kaɗa kan ta tana mai barin ɗakin , sautin ƙarar cumgum ɗin bakin ta tare da sauran kalaman da ta furta suna amsa kuwwa cikin kunnuwan yakaka ,"   To ita yanzu INA MAFITA ??? Tayi zurfi cikin tunani har bata san lokacin da falmata ta dawo ba , sai ji tayi tana ambaton sunan ta ," A sanyaye ta miƙa hannu ta riƙo hannun falmata ," tana buƙatar mashawarci tana buƙatar a bata ƙwarin guiwa akan abun da ta ƙudurta cikin zuciyar ta , toh sai dai bata da abokin shawara bata da kowa a tare da ita sai falmata ƙanwar ta , dan haka a karo na farko tayi niyyar ta buɗe zuciyar ta ga falmata duk kuwa da ƙarancin shekarun ta amma bata da haufi akan kaifin hankali tare da tsinkaye irin na falmatan wanda halitta ce ko kuwa baiwa daga Allah . falmata samy baby tace gobe zamu je a fidda min abun da yake ciki na ,! ta ɗora da warware mata duk yadda suka yi da samy baby da irin togaciyar da tayi mata na barin su da kan su idan har taƙi amincewa a fitar da cikin . Shiru kowaccen su tayi ,"    Yakaka ki bari mu haihu mu zama mu uku muma ,!     Ta tsinkayo kalaman falmata da suka sanya ta ɗan murmusawa ,"kalmar mu haihu ta bayyana ƙauna ta gaskiya da take tsakanin su abun da ke cikin ta ba nata bane ita ɗaya nasu ne su biyu da ƴar uwar ta,"     falmata idan mun haihu aina zamu zauna da yaro jinjiri ? kuma da me zamu yi rainon yaron ?        Zamu ajiye shi cikin jikin mu ruwa da rana da sanyi da iska baza mu bari su cutar da shi ba , zan yi bara na samo kuɗi muyi rainon sa , Lokacin da falta tayi irin cikin ki naji mamar su bakura tana cewa Allah ya sa kar ta zubar da cikin ta kashe yaron babu kyau babban zunubi ne ," Idan muka bar cikin nan kowa zai cigaba da tsanar mu , duk inda muka je za'a kore mu ,    muna da junan mu yakaka, kina da ni ina da ke , duk inda muke zamu kasance tare kafin abin da yake cikin ki ya fito mu zam mu uku , zamu haɗu mu zama rumfa agare shi har ya girma ,! Idan muka tafi wani garin da tace zata kai mu mun sake yin nisa da maman mu , watakila shikenan mun tafi baza mu dawo ba toh aina zamu ga maman mu ? Yakaka ban san ko kema kina jin irin abun da nake ji ba a kullum ji nake watarana zamu haɗu da maman mu tana nan bata mutu ba ,!   kar mu bar garin nan yakaka ! Amma ya zama dole mu bar gidan nan falmata !    Mu tafi ina ? Koma ina ne zamu tafi falmata . Toh yakaka shikenan ,! Shiru ya ratsa tsakani a hankali yakaka ta zame gami da kwanciya rigingine tana mai sake zufafa cikin tunani ,     Tun ranar da ta fahimci cewa tabbas fa tana ɗauke da ciki a jikin ta , taji wani  ƙaƙƙarfar so da ƙaunar aɓun da yake cikim nata yana huda zuciyar ta yana ƙaruwa a duk wayewar garin duniya ," ƙaunar sa tana sake ninkuwa idan ta tuno fa bature kam silum shine baban abun da yake cikin ta , wani farin ciki take ji a duk lokacin da ta tuno zata haifi ɗa mai irin kamannin sa ,watakila ma ya gado mahaifin sa wurin gayu da ƙwalisa , a jikin ta take ji watarana zai dawo gare ta , zata nuna masa ɗan sa ko ƴar sa , ko ya ƙarba abun da ta haifa ko kar ya ƙarba ,wannan ba damuwar ta bace ba , kamar yadda falmata tace , zasu yi rainon abun da ta haifa da dukkanin ƙarfin su , zata haɗa shi da falmata ta zamto garkuwa a gare su , zata zamto musu inuwar da zasu tsaya a ƙarƙashin ta su fake zafin rana da dukan ruwan sama , zata kasance bangon da zasu jingina su huta a jikin sa , zata yi kome domin ganin rayuwar su ta inganta , Tamkar abun da yake cikin ta yaji irin tunanim da take , sai ya harba a karo na farko ya fara motsawa a cikin mahaifar ta alamun da yake nuna a yau an busa masa numfashi !   a ɗan firgice ta kai hannun ta saitin inda taji motsin sa tayi kasaƙe tana son sake ji , ai kuwa sai ta ji zil-zil ya sake motsawa da ɗan karfi ," Da sauri ta kamo hannun falmata wacce take taɗin zuci ," ta ɗaga rigar ta tare da ɗaura hannun saitin cikin ,"   Falmata kin ji abun da yake ciki na ya fara motsi ,"    da sauri falmata ta sake manna hannun ta lokaci guda tana washe gajejjerun haƙoran ta , ta ina ne inda na ji ???? Suka dafe cikin tare        Sake yin ɗan ƙaramin motsi yayi , ai kuwa a tare suka saki ƴar sakakkiyar dariyar su ,tamkar masu gasa !         yaron mu INA SON KA , falmata ta furta hakan da sanyin murya da tattausan murmushi yakaka take kallon ta ,"         NI KUMA INA SON KI FALMATA NA . 5:20am Falmata falmata ,    yakaka ke tashin ta , jin an shiga sallar asubah ,'     tashi mu tafi lokacin tafiyar mu yayi !    toh yakaka ,    jakar baccon su ɗaya ta ɗaurawa falmatan a kai ita ma ta ɗau ɗayan bayan ta kullewa samy baby ɗakin ta ,tare da ajiye mukullin a ƙarƙashin shimfiɗar goge ƙafa da yake shimfiɗe bakin kofar ɗakin . Da bin bango suka fita a gidan suka miƙa bakin hanya hannayen su sarƙe da na juna , a tsorace suke sosai akan hanyar babu kowa sai jifa jifa suke cin karo da mutane zasu masallaci , zuciyar yakaka sai bugu take da fargabar gamuwar ta da karnuka . Da ikon Allah suka ƙaraso bakin babban titi , lokacin gari ya fara yin ɗan haske shaa ,' Alfijir ya keto ,' cikin nutsuwa suka tsallaka titin , yakaka tana mai waiwayawa kallon kwarin unguwar a ran ta tana jin har abada baza ta sake tako kafafun ta cikin unguwar ba ! . A cikin rumfar bakin wani shagon da yake jikin kasuwa suka yada zango , yakaka wacce ta gaji tilis da ƴar tafiyar da suka yi sakamakon rashin ƙarfin jiki , ta kwanta a dandaryar sumintin gaban shagon gami da yin matashi da baccon ta , falmata kuma ta zame ta zauna daga jikin bango ," Falmata ke zan ajiye ki wurin barar ki na da idan an fito kasuwa ni kuma zan ɗan kewaya na nemi wani ɗan aiki , ko dako ne ma nima nayi na ɗan samo mana wani abu kafin mu ga yadda Allah zai yi da mu koh ? hakane yakaka , amma ke ki zauna kawai kin san fa baki da isasshiyar lafiya kar ki je kiyi aiki kuma ki cutar da kan ki da yaron mu ,! bazan yi aikin wahala ba daidai karfi na zan yi falmata .   Toh shikenan yakaka . Suna nan zaune gari ya waye tangarai mutane suka fara kai kawo masu sana'ar safe suka fara hada-hada gasu nan iri-iri, nan yakaka ta hango wata mai sayar da ƙosai da fanke wanda ƙamshin suyar ta ya bugi hancin yakakar , nan take ranta ya biya ," falmata ga masu abin karyawa sun fara mai zan karɓo mana ? ki sayo mana duk abun da ran ki yake so yakaka ! to ki kula mana da jakar kayan mu sosai .     Toh Ƙosai ta saya tare da fanke , ta ƙarasa wurin wata mai sayar sa koko ta sayo masu , har zata wuce ta ga mai masa nan ma ta tsaya ta saya ," tace a zuba mata yajin ƙuli ya ji sosai ," nan aka baɗe mata kan masar da yajin ƙuli," Nan suka zauna suka ci suka gyatse , falmata ta sha ruwa daga randar da take daura da rumfar da suke,  yakaka tace ita baza ta sha ruwa yanzu ba domin tana sha amai zata yi , anan suka cigaba da zama suna ƴar hirar su jifa-jifa har zuwa tara na safe lokacin da ƴan kasuwa suka fara fitowa ," mutumin da yake mamallakin shagon da suka yada zango bakin sa , shi ma ya fito , da kallo ya fara bin su da shi cikin shakku da rashin yadda musamman da ya ƙƴalla ido ya ga baccon kayan su ai sai ya jaa baya , lura da shi yakaka ta yi dan haka ta fara gaishe shi nan falmata ma ta fahimci akwai mutum a wurin ita ma ta fara miƙo tata gaisuwar   amma maimakon ya amsa sai ta ga ya juya ya nufi wata ƴar hanyar da ta ratso tsakanin shaguna ya tafi ya bar su   Nan yakaka ta shaa jinin jikin ta ," Falmata kin ga wannan mutumin ƙila nan da muke zaune shagon sa ne , kuma muna gaishe shi naga ya tafi ya bar mu  " ko dai bai yadda da mu bane ? Tashi mu tafi kar ya ƙira mana hukuma a kama mu ., yakaka ta ƙarasa zancen tana miƙewa ," nan ita ma falmata ta miƙe , mu yi sauri mu tafi yakaka kar a kama mu ! Har sun fara tafiya suka ji an dakatar da su , ta hanyar daka musu tsawa tare da basu umarnin tsayawa ," Chak ! Suka tsaya zuciyoyim su na bugun lugude ,! [6/24, 10:59 AM] +234 701 013 7848: Mafari ....... ( Hargitsin Rayuwa ) umm'muaz 21 A tsorace suka juyo , yakaka tayi arba da wani mutum jikin sa sanye da shuɗin kaya hannun sa ɗaya rike da wata ƙatuwar kulki , gefen sa kuwa wannan mutumin da take zaton sun yi masauƙi a bakin shagon sa ne Nan take ran ta ya aina mata , ", ya ƙira musu jami'in tsaro ne ," dan haka ta matso falmata gami da sake riƙe hannun ta ƙam-ƙam , Daga chan inda yake tsaye yace ! Su waye ku ? Kuma daga ina kuke ? Meye kuma kuke tafe da shi a baccon hannu ku ?kuyi gaggawar sanar da mu kafin naje na kira sojoji . Mukut ! Yakaka ta haɗiye yawun tsoro . Mu mune su falmata kuma mu ƴan gudun hijira ne daga ƙauyen mairambiri , kayan mu ne a cikin bacco .     Falmata ta amsa musu cikin dakiya . Wanne irin kayan ? Kayan sawar mu .     Suka haɗa baki wurin amsa masa ! Ku buɗe mu gani ? filla-filla suka yi da suturun nasu , ba tare da gardama ba . Meyasa kuke yawo da kaya ? Ina ne sansanin ku ? Bai kamata kuna yawo da jakar bacco ba saboda kun san halin da gari yake ciki ba'a yadda da duk wani mutum da aka gan shi da kaya niƙi-niƙi kuma yana nuƙu-nuƙu a cikin taron jama'a bare ma ku yara mata ga kuma irin yanayin ku , kowa ya gan ku dole zai zarge ku har ma ya tsora ta , saboda yadda mafi yawancin lokaci ake amfani da ku ta hanyar rataya muku nakiyar bam ku shiga taro ku tayar , Ku godewa Allah ma lokacin da na gan ku a bakin shago na ba jami'an soja ko na ɗan sanda na kira ba mai gadin kasuwa ne , da ace ɗaya daga cikin jimi'an tsaro ne da sai sun hukunta ku dan haka nake baku shawara da ku koma sansanin ku , ku ajiye wannan jakar kayan naku sannan idan ma zaku shigo gari harkokin ku sai ku shigo , yawon ku a haka hatsari ne ga rayuwar ku ,! Duk wannan dogon bayanin da mutumin nan yake musu yakaka ta zurfafa cikin tunani , jin ya ambaci komawar su sansanin ƴan gudun hijira ,"       Cikin ran ta ta ƙudurce baza su koma sansanin su ba , saboda tun bata tare da ciki ma ƙuƙaƙƙiyar wahala ce zaman sansani ƴan gudun hijira , sanan ga tozarci uwa uba fyaɗe da ake yi wa mata , to bare fa yanzu da take ɗauke da cikin da bashi da uba , ta koma sansanin su a gan ta da ciki ,? Tace aina ta samo shi ? Alhalin duk wanda ya san ta ya san ta ne a matsayin budurwa wacce bata taɓa aure ba , ai ta tabbatar fanne baza ta bar ta ta kurɓi ruwa ba zagi da aibatawar da zasu dunga mata sai ya samar mata da cuta , dan haka gara sun hakura da zaman sansanin sun nemi wani wurin fakewar ," Da wannan tunanin ta ɗago kan ta ta dubi mutumin , da taji falmata na bashi amsa da cewa     Sun ɓata ne sun kuma manta sunan sansanin su . Malam dan girman Allah ka taimaka mana ka samar mana da wurin da zamu dunga kwana , " bamu da kowa a garin nan mamar mu da ƙannen mu sun ɓata tun a ƙyauyen mu baban mu ya mutu , mijina ma ba'a san inda yake ba ,"    Ta ƙarasa zancen tana mai sunkui da kai domin gujewa kallon rashin yadda da wannan mutumin yake jifan ta da shi ," cikin ranta kuwa kunyar sabuwar ƙaryar da ta gilla take yi ,     Saitin inda take jin tashin sautin muryar yakaka ,  falmata ta maida fuskar ta , cikin ran ta tana mamakin yaushe su duka suka koyi ƙarya ? ? Shiru yayi yana nazari , kwarai zai so ya taimakawa yaran ko dan kasancewar su mata , duk da cewa cikin ran sa ba wai ya gama aminta da zantukan su bane gaba ɗaya , toh amma shi ya san ba ƙaramar fitina zai tadawa kan sa ba muddin ya ɗauki yaran nan ya kai su gidan sa ya jefa su tsakanin matan sa uku ," yana da tabbacin sai an dafa su da ran su , shi kan sa ruwan gidan sai ya gagare shi shaa da kwanciyar hankali ,  dan haka da muguwar rawa gamma ƙin tashi . Yarinya ni bani da wajen da zan kai ku , ku samu wurin kwana saboda yanzu duniya ta lalace ba'a saurin yadda da mutum . Alfarma ɗaya zan muku shine na yadda duk lokacin da dare yayi muku kuna tsakanin nan bakin kasuwa ku gangaro cikin rumfa ta ku kwana bazan hana ku ba ,' har ma tabarma zan ajiye muku , bayan na sanar da masu gadin kasuwa wanzuwar ku awurin kun ji ko ? Ya furta hakan yana danne yanayin da yake ji na rashin kyautawa yana taso masa , ya san ba haka ya kamata yayi musu ba yasan taimakon da suke nema ya wuce wannan yasan bai ji tausayin su bai kuma basu kariya ba , toh sai dai yana jin iyakacin taimakon da zai iya basu kenan , Ga mamakin sa godiya suka dunga sauke masa kwando-kwando tamkar wanda ya basu wurin kwana a ƙuryar gidan sa , hakan ya sa tausayin su ya sake baibaye shi ,"    Ku dawo da jakar kayan ku ajiye cikin shago na ," kuma ku tabbatar kafin cikar karfe huɗu da rabi kun bar duk inda kuke kun dawo kun amshi kayan ku domin ni karfe huɗu da rabi nake rufe shago ," Cikin daɗin rai yakaka ta kawo falmata dai-dai wurin da take zaman barar ta ,'  ta ajiye ta bayan sun gaisa haba-haba da ɗan dattijon da yake sayar da kayan miya a gefen wajen wanda suka tarar da shi yana fidda kayan lambu ɗangin su yakuwa , alehu , zogale , rama da sauran kayan lambu yana shirya su akan ɗan teburin sa ga alama bai jima da isowa ba , har yake jajen kwanaki da dama baya ganin falmata ,"     Nan suka ce hana su fitowa aka yi daga sansanin su ,"       Falmata ga naira ɗari ki sayi wake da shinkafa da salat ki ci anjima da rana , kar ki ce zaki zauna da yunwa kin san bana so ," kuma kar ki tafi ko'ina , nima ba nisa zan yi ba zagayen kasuwar zan kewaya ko Allah zai sa na samu ko dako ne nayi na ɗan samo mana ƴan kuɗi kin ga ƙarshen kuɗin hannu na ne ɗarin da na baki , bayan ita bamu da ko sisi ki kula da kan ki sosai kin ji kou ? Naji yakaka ta furta hakan tana  mai miƙewa tsaye daga kan ɗan dutsen da yakakar ta ajiye ta , gaban ɗan teburin mai kayan miyan ta ƙarasa    Baba ɗan Allah ko zamu samu chanji ? Tana mai miƙa masa gudan ɗarin ,     Ƙarɓa yayi , ya bata hansin biyu ,ta ƙarba tare da lalubar hannun yakaka ta danƙa mata gudar hansin ɗaya , Idan kin bani duk kuɗin ke kuma da me zaki ci abincin anjima ? Kin fini buƙatar abinci yakaka , ke da baki da lafiya ,kar kiyi aikin wahala da yawa wanda zai sa ki samu matsala , idan kin shiga matsala ni kuma yaya zan yi yakaka ? Dan Allah ki lallaɓa kan ki , kuma ki dawo da wuri ," Toh madam falmata ta furta hakan tana murmushi jin yadda falmata ta zage tana bata umarni kamar dai ita ce babba . Hanya ta miƙe tana tafe tana raba ido cikin fatan son ganin inda zata ɗan samu wani aiki ta je ta kama ko da ba'a sa ta ba , amma har ta kai kan gadar kasuwar bata ci karo da wani wajen da ake buƙatar ƴan aiki ba , hasalima yanzu ne ƴan kasuwar suke kan buɗe shagunan su , tare da fito da kayayyakin sana'o'in su ," Har ta yanke shawarar komawa wurin falmata ta ɗan jira zuwa anjima , sai idanun suka hango mata mattatarar masu niƙa a ƙwarin gadar , Sai ta yanke shawarar ta ƙarasa wurin ƙila ta samu aikin yi tun da ta hango wajen a cike ," Gangarawa tayi ta sauka wajen , ga mamakin ta masu injinan niƙa ne birjik ta ko'ina a wajen , ƙarar inji kuwa ba'a cewa kome domin ko maganar na kusa da kai baka iya ji sai fa idan yayi ihu ,' Da gudu ta ga wasu ƴan matasan yara maza da baza su gaza falmata ba sun nufo ta ,"    Yaya ta niƙa ne ? Ki kawo na kai miki injin mu yau yau muka kai faifan injin washi , laushi luƙui za'a miki , Yaya ta injin su mutuwa yake ana cikin niƙa , anjin mu yafi lafiya kuma ga arhar niƙa ," Ita dai da ido take bin su da kallo ba sosai take fahimtar su ba , saboda ƙarar injin da ya cika mata kunne , Ita ma da ɗan karfi ta amsa musu    Ba niƙa na kawo ba , aiki nake nema ,    Haɗa ido yaran suka yi suka kwashe da dariya , suka maimaita    Wai aiki take nema ?  kut wannan ƴar na'u ce ita ma .   Juyawa suka yi suka bar ta nan tsaye ba tare da sun bata ansa ba . Har sun ɗan yi nisa sai kuma ɗayan ya komo , aikin tankaɗe dusa kike nema ??     Batare da ta kai ga fahimtar sa ba ta gyaɗa kai ,     Zo muje injin abokin yayana jiya sun ɓata da mai yin tankaɗen dusar sa ,     Da murna yakaka ta bisa a baya har wata ƴar siririyar hanya , bayan ƴar gajerar tafiya suka bullo a wani babban fili faffaɗa , saɓanin injinan da ta tarar a waje waɗannan manyan injina ne girkakku , ƙaran su mai matuƙar karfin gar diri yake a cikin ƙasa ," Gaba yaron yayi zuwa wurin wani da yake tsaye a gefen ɗaya daga cikin injinan yana juye hatsi a cikin injin bayan ya gwamtsa shi da ruwa . A kunne yayi masa maganar yana mai nuna yakaka da ɗan yatsan sa ," Bayan sun gama magana ya dawo wurin yakaka ,'      Yace wai shi ba zai biya ki ko sisi ba dusar da zaki tara ita ce ladan aikin ki ," kin yadda ?    Cikin sanyin jiki yakaka ta gyaɗa kan ta , "bata da zaɓi ! Amma cikin ranta tana tababar ta yaya dusa zata zama ladan aikin ta me zata yi da dusa toh ? Ko suna nufin ta ci ??    Bayan yaron ya faɗa masa amincewar yakaka , da kan sa ya taso ya zo inda take ,      Keh yane ƴar na'u ? Kin gane ne aikin yana da yawa dan haka zaki samu alheri , ina ga nima har sai kin ware min wani abu a ciki , ya ƙarasa zancen yana kwashewa da wata hautsinannan dariya ,      Biyo ni na nuna miki aikin , Cikin wata babbar rumfa ya kai ta , wacce take cike da mata tsoffafi da ƴan mata irin ta da ma waɗanda suka fita , wasun su a tsaye suke suna faman zirta hatsi , masara , dawa , alkama , a manyan-manyan turamen da suke watse a cikin rumfar , wasu kuma suna zaune a ƙasa suna ta faman bushe abun da suka zirtan , suna tara dusar a buhun gefen su ," Wani babban buhun masara da na hatsi ya nuna mata ,"   Ƴar na'u wannan ne aikin ki yau ake so , kiyi aiki mai kyau dan gaba a neme ki , kuma banda waskiya ai kin gane ?  idan masu shi suka kama ki kin waske musu abun su , suka ciya miki ni babu ruwa na ai kin gane ko ?   Na gane Toh ki zo mu je na baki aron faranti dan naga baki da shi , kuma waɗannan ƴan ciki baki baya kwalta ne , ba baki aro zasu yi ba ! Zungui zungui ta bishi a baya ,' Daka da surfe ba sabon abu bane wurin yakaka , toh bare wannan da zirtawa ne ba surfawa ba , manyan injinan su ke yin surfe ," nan take ta kama wani turmi da ta ga babu kowa akan sa , ta ɗauki wata ɓasgararriyar taɓaryar da take jefe a gefe ta kama aikin ta babu tsayawa hira , to ma wa ta sani a wurin da har zasu yi hira?? Babu ! Kafin la'asar yakaka ta zirce hatsin da masarar tas , ta hau bushe dusar har da gyarawa , la'asar lis ta gama ta tara dusar daban-daban fiye da rabin buhu kowannen su , iyakar gajiya ta gaji , ga yunwa ga kishirwa , nan gefen ɗan buhun ta samu ta zauna tana mayar da numfashi ,  dayawa daga matan sun gama aiyukan su suna zaman hutawa ,' Ba'a jima ba masu kayan suka zo ɗauka ƙarƙashin jagorancin "ubangidan ta "mai surfen , nan suka duba kayan su ," yakaka ta jawo buhun dusar ta nuna musu ,   Ɗan saurayin da ya zo ɗaukar kayan ya ciro naira ɗari biyu ya miƙa mata ya ce ta haɗa da dusar ta riƙe kamar yadda suka saba , Da murnar ta ta sanya hannu biyu ta ƙarbi kuɗin , cikin ran ta tana tambayar kan ta toh ita kuma me zata yi da dusa ? Ina zata kai ta ? Tunanin ta ya katse lokacin da ta ga wasu dattawan maza da mata sun fara shigowa , da gudu ta ga kowacce mace tana surar buhun dusar ta tana kaiwa gaban su ," wannan tace tata ta masara ce , wannan ta ce ta hatsi , wannan ta dawa , alkama , su kuma suna tambayar kwano nawa ne ?? ko kuma daro nawa ?? Sai ta ga an fara cinikin dusar , ita dai tana tsaye tana bin su da ido cikin son fahimtar abun da suke , Kafin kace meye wannan tas mutanen sun gama saye dusar nan har sun fara lodawa a wulbaro ana jide musu , fahimtar da tayi masu sayan dusar ne , ya sa ta janyo nata buhun-hunan ta kawo gaban su ," Cikin tsanaki ɗan dattijon yake kallon ta duk alamun gajiya da yunwa sun bayyana a gare ta fatar bakin ta har ta bushe , jikin nan busu-busu da ƙurar dusa ,"   Kwano nawa ne ƴan mata ? Nima ban sani baba Ungo wannan daron hashimu juye ka auna dusar yarinyar nan kwano nawa ne ," Tana tsaye aka auna kwano biyar biyar ne , ta masarar da ta geron , Kuɗin ki naira ɗari huɗu ne ƴan mata kowanne kwano murtala biyu muke sayan sa idan dusa mai nawi ce irin taki , idan kuwa faya-faya ce naira ishirin da biyar ne kowanne kwano , Ɗari biyar ya miƙa mata tare da buhun ta ,'     Bari na nemo chanji baba ta furta hakan tana jin wani zallar farin ciki kamar tayi tsalle ," Ki bar chanji yarinya ki sayi abinci da ruwa ki sha , ki daina zama da yunwa a wannan halin da kike ciki babu kyau , Allah yaye mana talaucin da ya addabi ƙasar mu ! Har ƙasa yakaka ta sunkuya tana jero kalaman godiya kamar zata kwanta ," Sauri sauri ta wanke jikin ta tare da ɗaura alwala da ruwan randunan ƙasa da ta gani birjik a filin wajen , ta lura har babban bayan gida ne a wajen wanda ake shiga a yi wanka da kama ruwa bayan an gama aiki , Gudu-gudu tayi sallolin ta na azahar da la'asar , ta ninƙe buhun ta ta cusa shi a ɗan wani lungu , ta fito tana kallon rana yadda ta tafi tana gaf da faɗuwa , hankalin ta baki ɗaya yayi kan falmata , A haka ta kama hanyar kasuwar busu-busu da ita sai cin karo take da mutane waɗanda su ma suke cikin sauri domin su bar bakin kasuwar , A zaune ta tarad da falmata inda ta ajiye ta tayi shiru da ita ta sunkui da kai , mafi yawancin mutanen da suke hada-hadar su a wurin duk sun watse hatta baba mai kayan miya baya nan," Cikin sauri ta dafa falmata ,"    Falmata na dawo , Yakaka kin dawo sannu da zuwa , baki gaji sosai ba koh ? Baki yi aikin wahala ba ko ? Kin ci abinci ? Ya jikin naki ?     Ƴar dariyar ƴake tayi , tana mai jin yadda jiri ke kwasar ta , ƙarfin hali kawai take wurin tsayuwa akan kafafun ta ,   Falmata tashi mu ƙarasa rumfar da zamu kwana kin san fa mutumin nan cewa yayi kar mu wuce karfe huɗu da rabi , yanzu kuma ina ga kamar biyar ma ta ɗan wuce kin ga kar ya fasa taimakon mu da yace zai yi mu dunga kwana a bakin shagon sa ,: A tSaye suka tadda shi a gaban rumfar shagon sa sai faman duba agogon hannun sa yake ," ba dan yadda yake jin tausayin yaran ba da tuni yayi tafiyar sa domin a ka'idar sa baya wuce karfe huɗu da rabi a kasuwa , sai ga shi yau har biyar da wajen minti ishirin , cikin ran sa ya aiyana ya ƙara musu mintoci goma idan basu zo ba zai yi tafiyar sa . Sai gasu sun iso ,     A gurguje ya ansa gaisuwar su ya shiga shagon sa ya fiddo musu da jakankunan kayan su gami da tabarma mai biyu da kuma wasu robobin abinci da suke rufe guda biyu , sai jakar ruwa ɗaya , yayi musu sallama bayan ya gargaɗe su a Kan su kula da kan su ," Ga mamakin yakaka sai ta ga ya sauke  musu jibga-jibgan labulen da aka yi da yadin tamfol duk kusurwa uku na rumfar wanda aka yi domin kare zubar ruwan sama zuwa cikin rumfar , kirif suka rufu daga barin idanun mutanen da suke kai kawo ba za'a san ma da mutane a ciki ba idan ba leƙawa aka yi ba , yana daga waje yayi musu sallama akan sai da safe , suka bishi da doguwar addu'a tare da godiya ! Cikin jim daɗin karamcin da yayi musu yakaka ta shimfiɗa musu tabarmar tare da kama hannun falmata ta zaunar da ita a gefen jakar kayan su daga jikin bangon shagon sai lokacin ta lura da ledar mai ɗan girma da take hannun falmatan ," Falmata menene wannan a cikin ledar hannun ki ??    Abincin ki ne yakaka , naga yanzu kin fi son tuwo miyar yakuwa shine na saya miki lokacin da naji baba mai kayan miya yace mai abinci ta kawo mishi , shine nima na bada kuɗi aka kawo miki , na naira ɗari da hamsin ne , ga sauran kuɗin da na samu yau ƙirga ki gani , "ta miƙa mata ledar da ta tara kudin a ciki , Da tarin ƙaunar ta da tausayi ta karɓi kuɗin ta kirga su naira ɗari hudu da sittin ne idan aka haɗa da kuɗin abincin da ta saya mata ya zama ɗari shidda da goma , ai kuwa lalle sun samu kuɗi ita ma ga nata naira ɗari bakwai hansin ɗin safe na abincin ta, kuɗin su sun kama dubu ɗaya da ɗari biyu da goma ," Falmata nima na nayi aiki na samu kuɗi har ɗari bakwai kin ji su , ta ɗora mata kuɗin akan hannun ta , da murna ta shafa kuɗin kai yakaka amma wallahi mun ji daɗi kin ga sai muyi ta tara kuɗin da zaki dunga zuwa asibiti ana duba lafiyar yaron mu kamar yadda likita ranar ya faɗa ," kuma mu dunga ware ko ɗari ɗaya ne kullum muna ajiyewa dan mu sayi kayan jarirai koh ? Idon ta cike da ƙwalla ta ce hakane falmata kin kawo shawara . Bari na ci abincin yunwa nake ji sosai falmata , ke ma ki ci wanda mutumin nan mai kirki ya bamu ga shi har kwano biyu , ɗayan sai mu bari da safe mu ci koh ? Ni ban jima sosai da cin abinci ba yau sau biyu na ci abinci na saya da hansin ɗin safen kuma baba mai kayan miya ma ya saya min biski da miyar yakuwa naci ɗazu da la'asar ,' anjima da dare kafin muyi bacci sai mu ci wannan ɗin , yanzu ni sallah nake so nayi ,! ****** Dare ya tsala yakaka ta gaza yin baccin kirki daga ta fara sai ta farka,  sai juyi take yi ta tattake a cikin abun rufuwar ta tayi matashi da jakar kayan ta , Ba kome ne ya hana ta bacci ba illa ciwon baya da kai , ga kuma matsanancin tsoron karnuka da take jiyo kukan su kurkusa da inda suke , zuciyar ta sai dakan lugude take , A hankali ta zira hannu ta lalubi wurin da falmata ke kwance , wayam ta ji bata nan , sake baza hannun ta tayi , ba shiri ta bankaɗa abun rufuwar ta gami da miƙewa zaune , duhu ne bakikkirin a cikin rumfar har ba'a iya ganin tafin hannun , murya ƙasa-ƙasa ta kira sunan falmata ,"    Shiru ta ji Da ɗan ƙarfi ta sake kiran sunan tana mai miƙewa tsaye ,     Haske ta ga ya ratso rumfar kafin ta ga shigowar falmatan tana lalube , da sauri ta taka ta kamo ta zuwa cikin jikin ta ta riƙe , murya ƙasa-ƙasa tace    Falmata ina kika je ? Meyasa kika fita ? Ke bakya tsoron dare ne ?   Yakaka fitsari na ɗan je baya nan nayi ba nisa sosai ba Meyasa baki tashe ni ba ,? Kar ki sake irin haka , ba a cikin gida muke ba a bakin kasuwa muke bakin titi cikin rumfa , babu kowa sai mu kaɗai !     Toh ta amsa mata Daga haka suka kwanta ƙwaƙume da jikin juna ko yaya ɗayan su ya motsa ɗayan zai iya ji ," Asubar fari suka tashi suka yi sallah suka ɗan sake kwanciya zuwa lokacin da gari zai ƙarasa wayewa ai kuwa waɓi daddaɗan barci ya kwashe su tare da taimakon sanyin asuba ba su suka farka ba sai da hayaniyar jama'ah da ƙarar motoci ya fara yawa wuraren takwas da rabi ,   Yakaka mun yi bacci dayawa , cewar falmata    Mu wanke baki mu ci abincin ALLAH ya sa bai lalace ba , ilai kuwa suna buɗe robar warin lalatatcen wake da shinkafa da miyar ya bigi hancin su ba shiri suka maida murfin , Bari na fita na sayo mana abin karyawa me zaki ci ? Fanke ko ƙosai ? Ko doya ko masa ? Ni kawai duk abinda zaki ci yakaka , ki nuna min wurin da zanje na zubar da abincin nan na wanke masa kwanukan ? Kwanci tashi suka yi kwanaki a bakin kasuwa suna gudanar da al'amuran su cikin jin dadi , ƴanci tare da walwala , sosai rayuwar da suke yi a bakin kasuwa ta fiye musu duk wata rayuwar da suka taɓa yi a cikin birnin maiduguri daɗi da kwanciyar hankali , zasu ci su sha kuma su adana ƴan kuɗaɗen su , babu ƙyara babu tsangwama , Ka'in da na'in yakaka ta kama aikatau ɗin ta ta riƙe kullum a chan take yini tana aiki chan take cin abincin rana , sai yamma lis take komawa gida , tayi wankan ta fes a banɗakin wurin aikin ta , a hanya zata ɗan saya musu ƴan kayan gwari da ake yayin su lokacin , karas ,lemo ,cashut da sauran su , Falmata kuwa har ta gane hanya daga wurin barar ta zuwa ƴar rumfar kwanan su , dan haka ta daina jiran yakaka ta zo ta mayar ta , daga ta ji kasuwa ta fara alamun watsewa sai ita ma ta tafi bakin rumfar ta jira zuwan yakaka , a hankali har suka fara sabo da jama'ar kewayen wurin , Yau an tashi garin a ɗan hargitse sakamakon kwana da aka yi ana ɗauki ba daɗi da ƴan tawayen boko haram da suke neman shigowa garin ta karfi ta wani yanki , sai dai basu samu nasara ba dakarun soji sun tarwatsa su wanda hakan ya jaa dayawa daga cikin su sun fantsama cikin gari da hakan kuma yake babbar barazana ga rayukan al'umma .   Saboda ɗaukar mataki sai soji suka fantsama cikin gari , tare da sanya dokar hana zirga-zirgan motoci akan manyan titunan garin , kasuwar kan ta yau ba'a buɗe ta ba duk inda ka bi motocin soji ne suke kai kawo , Jugum-jugum falmata da yakaka suka yi , su sam basa ƙaunar wannan jiniyar ta motar sojoji , tsinka musu zuciya take ta tada musu hankula kamar yadda ya faru a yanzu tun safe sun gaza ko cin abinci sai faman wuri-wuri suke , ko ƙwaƙwarar magana sun gagara yi da junan su , illa hannun su da yake cikin na juna , lokaci zuwa lokaci yakaka tana ɗan leƙawa ta tsaƙanin labulen rumfar su tana ganin yadda garin yake shal tamkar an share . Sun kwashe tsawon lokaci a haka , har zuwa lokacin da suka ji an kamo wasu gungun mutane an wuce da su ana ta dukan su , Basa fahimtar maganganun da suke tashi a wurin illa dai suna jin ana yawan ambaton kalmar boko haram , boko haram , boko haram ! Yakaka ta so leƙawa ta ga ko su waye ,? Amma sai ta ji falmata ta sake damƙe mata hannu , ƙasa ƙasa ta ji tace     Yakaka kar ki leƙa , tsoro nake ji , zuciya ta bugawa take , yakaka mu yi addu'a kar su gan mu su kashe mu . Wucewar mutanen bai fi da mintoci biyar ba suka ji ƙarar fashewar bam da matuƙar ƙarfi har sai da rumfar da suke ciki ta girgiza , Harbe harben bindigogi ya biyo bayan tashin bam ɗin tare da guje -guje har ta gaban rumfar su suke jin takun gudun mutane tare da wucewar harsashi ," Iyakacin ruɗani tare da tashin hankali sun shiga kuka suke yi suna tsaye charko charko cikin rumfar ," Suna nan tsaye falmata ta ji wani ƙaƙƙarfan abu ya bugi kafaɗar ta ya wuce wanda sai da ya sa tayi baya da karfi ta bugu da jikin kofar shagon kafin ta silale ƙasa , cikin wani irin azabar raɗaɗi da take ji yana gauraya illahirin jikin ta takamaimai bata san ina ne yake mata ciwo ba , a razane yakaka ta jiyo jin yadda hannun falmata ya kufce daga cikin nata , abun da tayi arba da shi ya sa zuciyar ta ta tsaya da bugawa , bata san lokacin da ta zube a ƙasa ba tare da tallafo falmata wacce jini ke malala daga jikin ta , idanun ta suna rufuwa su buɗu da kan su , jikin ta kuwa babu inda baya rawa ,.'   Falmataaa ta kira sunan ta da wata irin murya tamkar ba tata ba , wani irin ihu ta kurma lokacin da ta fahimci abun da ya faru ,.......!    Masha Allah ina gaida masoyan littafin mafari a duk inda suke ! Vote Share Comments            [6/24, 10:59 AM] +234 701 013 7848: MAFARI ( Hargitsin Rayuwa ) umm'muaz 22 Da gudu ta tako ta fito daga ƴar rumfar , yanayin da ta ga falmata a ciki ya mantar da ita duk wani halin fargaba da tsoron soji da suke ciki , Tana kuka ta nufi bakin titin inda ta hango gungun soji da wasu mutane farar hula suna tsaye , tun kafin ta karaso gudun da ta taho da shi ya ɗau hankalin su ,tare da ihun da take faman yi Tana ƙarasowa ta zube a gaban su ba tare da ta ji tsoron bakin bindigar da ta ga sojojin suna gyarawa ba tare da saita ta da ita ,"     Da rishin kuka take cewa kun harbi ƙanwa ta , zata mutu , kun kashe min ƙanwa ta me tayi muku ? Mu ba boko haram bane , meyasa zaku harbe ta wayyo Allah ƙanwa ta ," Wasu daga cikin su sun fahimci abun da tace dan haka wani daga cikin su fararen hula ya ɗan matso kusa da ita ,     Ina ƙanwar taki take ? Waiwayawa tayi tana nuno masa ƴar rumfar da suke ciki , tsabar kuka da ruɗanin da take ciki har numfashin ta sarƙewa yake yi , Su biyu suka nufi rumfar    Yakaka ta take musu baya Nan take suka fahimci bullet ne ya samu falmata a kafaɗa cikin rashin sani ," Da gudu gudu suka koma wajen sojojin tare da neman taimakon su akan a kai yarinyar asibitin kurkusa , ba tare da gaddama ba soja ɗaya ya amince zai jaa su a motar su ta soji . Dan haka suka ciccibo falmata wacce ta riga ta suma suka ɗora ta bayan hilux ɗin sojin tare da yakaka wacce idan banda sambatun kiran sunan falmata babu abun da take gaba ɗaƴa ta ƙanƙame falmatan a jikin ta . Da isar su babban asibitin gwamnatin jaha ( general hospital ) wanda bashi da wani tazara mai yawa da bakin kasuwar , aka shige da falmata bangaren bada taimakon gaggawa ( Accident and emergency)  nan suka tarar da mutane dayawa da suke cikin hali makamancin na falmatan wanda tarzomar jiya ta ritsa da su birjik , wasu sun ji munanan raunika , wasu babu hannu , wasu ba ƙafa , likitocin da suke kan aiki sai kai kawo suke , da alama sun gaji likis ga har zuwa yanzu akwai waɗanda ko kai ga fara basu taimako ba'a yi ba , Nan suka ajiye falmata akan dandaryar siminti bakin kofar domin duk gadajen da suke cikin ɗakin a cike suke , Bayan sojan ya shiga ciki yayi musu bayani , likitocin suka ce a ajiye ta kawai zasu zo kan ta domin aiki ya musu yawa , ko kuma idan likitocin safe sun zo su duba su tun da sun ce harsashin a kafaɗa ya same ta da sauki akan waɗanda bam ya tashi da su , Tsayuwar da bata fi ta rabin awa ba mutanen da suka kawo su suka yi , suka matso kusa da yakaka wacce har zuwa lokacin idanun ta zubar hawaye suke har sun kumbura ,      Yarinya mu zamu tafi , domin muna da aiyuka a gaban mu , su kuma likitocin nan ƴan walakanci ne basu da niyyar zuwa su duba ta , ki cigaba da jiran su , sannan ki dunga leƙawa kina damun su akan su zo su duba ta , idan kuwa ba haka ba har jinin jikin ta sai ya ƙare ta mutu anan indai likitocin nan ne babu abun da ya dame su , mu mun tafi , ga wannan ki rike a hannun ki ko zasu ce ki sayo wani magani ,suka miƙa mata dubu ɗaya suka kaɗa kan su suka yi ficewar su ba tare da sun sake kallon inda falmata take yashe a ƙasa ba ," Wani sabon kuka ta sake fashewa da shi tana tattaɓa fuskar falmata wacce tayi sanyi ƙalau ,"     Falmata na dan Allah kar ki bar ni , Falmata dan Allah ki tashi ,'   Kamar mahaukaciya ta yunƙura ta tashi ta bazama ta faɗa cikin ɗakin da ake duba marasa lafiyan ,"    Tana shiga nurses ɗin da suke taya likitocin aiki suka yi mata chaa ,"    Mata meye hakan ? Baki ga aiki muke ba zaki zo kan mu da ihu ? Ki koma daga waje ki jira a fito da marar lafiyan ku , ba'a shigowa nan idan ba mu muka kira mutum ba fita-fita dallah ,"   Kuka ta fashe da shi    falmata na zata mutu dan Allah likita ki zo muje ki duba ta jini sai zuba yake daga jikin ta jinin ta zai ƙare ta mutu idan ta mutu bani da kowa ,"     Kalaman ta suka doki kunnuwan sa yayi tsai daga aikin ɗinkewa wani mutum mummunan rauni da yake yi ,"     Tabbas ita ce , ita ce da kullum damuwar ta yake ga falmata ƙanwar ta ita ce da kullum hawayen ta yake zuba akan ƙanwar ta falmata , bata da wani abu mafi muhimmanci da ya wuce ƙanwar ta falmata , ita ce wacce ya kwashi watanni yana neman ta har ya zo ya haƙura ,    Cikin nutsuwa ya waiwayo yana duban inda take lokacin da nurse ɗin ta sanya wata security guard da take tsaye daga bakin kofa , tayi waje da ita domin tana son bata musu aiki ,"     Security guard ɗin ta cukuikuyo hijabin ta tana tura ta waje ,    Ita kuma tana sake ƙara karfin kukan ta tare da neman su taimaka mata ƙanwar ta kar ta mutu ," Hey jumai let her come in . Suka tsinkayi muryar babban likitan su da yake duty , ya bada umarni A tare suka waiwaya da yakaka wacce jin muryar sa ya sa ta waiwayo da fatan son kasancewar shi ne da gaske a wurin ai kuwa tayi arba da shi jikin sa sanye da korayen kaya ,'ɗan siririn farin gilashin da yake ɗore saman karan hancin sa bai isa ya sa ta gaza gane shi ba ," Da ƙarfi ta fizge jikin ta daga riƙon da security tayi mata , ta tako da gudun gaske ta ƙurɗo ta tsakanin gadajen marasa lafiya tana zuwa ta kamo hannun sa da yake cikin safar hannu ta duba marasa lafiya ta shiga jaan sa tana cewa     Dakta ƙanwata falmata ai ka san ta ko ? Ita ce harsashin bindiga ya same ta , ta suma kamar ta mutu jini yana ta zuba a jikin ta , dan Allah ka zo muje ka duba ta ,kar ta mutu dan Allah ka taimaka min !   A hankali ya zame hannun sa daga riƙon da tayi masa , ya maida duban sa ga nurses ɗin da suke tsaye    Ku sa a shigo da ita ! Doctor bamu da gadon da zamu ajiye ta ,"     Yana mai komawa bakin aikin sa yace      A nemo gado a ɗaura ta akai yanzu zan duba ta ,'    Biyu daga cikin nurses ɗin suka fita tare da security guard ɗin , yayin da ɗaya ta aunawa yakaka harara ,    Ai Sai ki fita mata , domin ba'a tsayuwa anan ,'    Ba tare da ya juyo ba yace Sister kalsum ki bar ta ta tsaya anan , yanzu za'a shigo da ƙanwar ta ,! Tashin hankalin da ya hango a fuskar ta ya taɓa masa zuciya sosai ,"yana jin  tausayin ta mai ƙarfi yana taso masa , ita kullum a cikin kuka da wahala take ! Mokaɗe baki nurse kalsum tayi ,    Cikin ran ta tana son sani alaƙar dactor hamza da wannan kucincinannar yarinyar ƙazama ! Cikin mintoci goma sai ga falmata an turo ta a gadon marasa lafiya an shigo da ita ," da hakan ya zo dai-dai da kammala aikin da yake yi ,    Ya tako ya zo gaban gadon falmatan ya duba ta tare da yin aune aune , nan ya fahimci ta zubda jini dayawa da ya sa dole sai anyi mata ƙarin jini , bayan an cire harsashin da yake cikin jikin ta    Dan haka yayi umarni a kare gadon falmatan a kuma sauya mata kaya zuwa na tiyata," sannan ya juyo da ganin sa ga yakaka , cikin tausasa murya tare da sigar lallashi yace ,       Ki nutsu ki daina kuka haka kin ji ko ? Ki samu wuri ki zauna a waje ,ki sayi ruwa ki sha ,insha Allah babu abun da zai samu ƙanwar ki , ɗan rauni kaɗan ta ji kuma yanzu zan cire mata harsashin na ɗinke mata wajen na sa magani zuwa anjima zata farka kuyi magana kin ji ko ?    Gƴaɗa kai tayi tana duban fuskar sa  cikin son samun tabbaci ta ce " Ka ce zata samu sauki har ta tashi anjima koh ?     Sosai kuwa insha Allah ya bata ansa yana mai duban ƙwarar idanun ta da tsabar kuka ya sauya musu launi ,"     da jan ƙafa ta fice tana waiwayan inda falmatan take ,    Shi kuma ya juya ya ɗau wata ƴar takadda yayi rubuce rubucen sa ya kira ɗaya daga cikin ma'aikatan da suke tura gadajen marasa lafiya/kujerar marar lafiya , ɗauko file da sauran su , ya miƙa masa takkadar bayan yayi Signature ya buga Stamp .       Ka je blood bank ka kai musu , ka tsaya ka ƙarbo jinin ka kawo .     Toh sir   Cikin gwanancewa ya fara aiki ga falmata !   Bayan awa ɗaya ya kammala ya ɗaura mata jinin da aka kawo leda ɗaya bayan yayi mata allurai ,     Sai da ya sake jaddadawa nurses ɗin da suka karɓi aiki akan su kula da ita Ƙanwar sa ce ,  bayan yayi bankwana da likitan da ya ƙarbe shi a bakin aiki ya shigar masa da duk wasu bayanai akan marasa lafiyan da ya duba ciki har da falmata da ya roƙi Alfarma a lura da ita da kyau , abokin aikin nasa ya amsa da zai kula da ita sosai .        Cikin takun da yake nuna tsabar gajiyar da yayi ya fito daga ɗakin , yana goge ruwan hannuwan sa da ya wanke da farin ƙyalle .        Tana hango fitowar shi ta miƙe daga inda take durƙushe a jikin bango ta nufo shi ,"         Cikin nazari ya tsaida idanun sa akan ta tana tahowa yana son tabbatar da zargin sa akan alamomin masu juna biyu da yake gani tare da ita alhalin shi a budurwa ya san ta . Dakta ta farka ? Tana magana ? Jinin ya daina zuba daga jikin ta ? Ko na shiga na gan ta ??       Bin fuskar ta da tayi jazur da kallo yake yana ganin yadda fatar bakin ta ta bushe idanun ta suka kumbura, Bai amsa mata tambayoyin ba ,  yace mata    Zo muje ! Ta bishi a baya tana waiwayen ɗakin da falmata take ciki , so take tayi gaddamar bin sa sai dai ta kasa , A bakin wani ɗan shagon da ake sayar da kayan sanyi da kayan fulawa irin su Biscuits, cake , meat pie , donut da sauran su , suka tsaya    Duban sa ya mayar kan fuskar ta cikin kulawa yace me zaki ci marar nawi sosai ? Zaki sha Hollondia yogurt  ? Ko juice kika fi so ? Cake zaki ci koh meat pie ?   Wani jirkitatcen kallo ta yi masa , falmata tana cikin yanayi irin wannan har shi yana tunanin zata iya cin wani abu ? Ai ita ko ruwa baza ta iya sha ba idan ba ta ga farkawar falmata cikin ƙoshin lafiya ba .   Sunkui da kan ta tayi daga kallon fuskar sa ,' cikin siririyar murya tace     Bana cin kome bana jin yunwa , dakta dan Allah ya jikin falmata ? Ta samu sauki , ka kai ni na gan ta dan Allah ,     Bai amsa mata ba sai ya maida ganin sa kan mai shagon da yake tsaye  ta cikin ɗan shagon sa yana kallon su .     Bamu hollondia yogurt babbar roba ɗaya da Chii exotics babba ɗaya , meat pie guda uku , tare da ruwan roba guda ɗaya .     Suna tsaye ya haɗa a leda ya miko musu , dakta hamza ya karɓa gami da miƙa kuɗi aka bashi chanjin sa , A takaice yace mata   Mu tafi ! Yana mai yin gaba   Cikin ƙosawa ta bi shi a baya . Wurin da motar sa take ajiye a wajen tsayuwa na musamman ya ƙarasa , gami da buɗe motar ya shiga   Ita ma yayi mata umarni da ta shiga bayan ya buɗe mata ɗayan bangaren ,"   Ta shiga ta zauna gami da mayar da kan ta jikin murfin motar ta kwantar tana jin wani irin yanayi marar daɗi yana taso mata , sam ita bata son takurar da yake yi mata a koyaushe idan suka haɗu ,!    Ledar da kayan da ya sayo suke ciki ya ɗora mata akan cinyar ta .     Bana son musu ko doguwar magana ki cinye kuma ki shanye duk abinda yake cikin ledar nan , ƙanwar ki na mata aiki na bata magunguna yanzu haka bacci take daga ta tashi zaki ganta insha Allah baza ta ɗauki lokaci mai tsawo ba zata warke, idan har kun zauna an bata kulawar da ta dace baku gudu ba ! Sanyin kayan da suke bisa cinyar ta suka haɗu da jin daɗin cewar falmata tana raye an yi mata aiki har ma tana bacci suka tayar mata da kishirwar da ta jima tana ji ,    Ba tace kome ba , ta buɗe ledar gami da ɗaukar gorar ruwan ta kunce bakin ta kafa kai ta fara sha bayan ta muskuɗa ta juya tana fuskantar murfin motar ta bashi baya ," Ajiyar zuciya ya sauke yana jin farin cikin sake ganin ta yana ratsa shi , ya zubawa bayan hijabin ta ido da duk jinin falmata ya ɓata , '    A garin yaya harsashi ya same ta ?   Ya jefa mata tambayar lokacin da ya ga ta gama shan ruwan ," Muna cikin rumfa ne a bakin kasuwa Bakin kasuwa ? ya maimaita    Me kuke a bakin kasuwa a wannan yanayin da gari yake ciki na hargitsi ? Daman anan muke zama    Ta amsa masa Kamar yaya ? Yaushe kuka dawo garin ?    Ɗagowa tayi ta dube shi Daman muna gari , a bakin kasuwa muke kwana a cikin rumfar mai shago !   Ji yayi kan sa ya wani irin juyawa , take alamun da ya gani na masu ciki a tattare da ita ya faɗo masa cikin rai ! Shi ƙwararren likita ne wanda ya san aikin sa ya kuma faɗaɗa tare da zurfafa bincike cikin duk wani ilmi da ya shafi lafiyar ɗan adam , ba sai wani ya faɗa masa ba ba kuma sai yayi gwaji ba babu shakka cikin kallon tsanaki da yayi wa yarinyar ya fahimci tana da juna biyu , toh amma ta yaya haka ta faru ? Wani mummunan tashin hankali ya ziyarce shi lokacin da yayi hasashen abun da ya faru ga rayuwar yarinyar , da ta yadda aka yi ta samu cikin   Tare da waye kuke kwana a bakin kasuwa ya tambaye ta yana tsare ta da kallon tuhuma .    Mu kaɗai ni da falmata ! Bai san lokacin da ya birkito da ita tana fuskantar shi ba ,"      Wacce irin rayuwa kuke yi a bakin kasuwar ? Baki da lafiya faɗa min waye yayi miki ciki ?      a tsorace ta ɗago kan ta tana kallon sa , yadda taga jijiyoyin kan sa sun tashi idanun sa sun kaɗa sun yi jaa ya sa ta matuƙar razana ," Nan take hawaye suka ɓalle a idanun ta , ta sake maƙure kan ta da jikin kofar motar    Sakin hijabin ta yayi tare da yin baya da kan sa ya ɗora a jikin kujerar da yake zaune bisa ya runtse idanun sa , tunani iri-iri suka rikito masa ,         Wani ƙazamin ɗan iskan ya riga ya bata rayuwar yarinyar tun a ƙaracin shekarun ta , mutanen  duniya mafi yawan su azzalumai ne , sun cutar da rayuwar yarinyar saboda rashin galihun ta , ji yayi zuciyar sa ta raurawa idanun sa sun kawo ruwa ," wani irin tausayin ta da ya danne tasirin bacin ran sa da zafin kishin da yake ji ,ya mamaye ruhin sa , Allah sarki talaka !   Ya furta a cikin ran sa ,     Murya ƙasa ƙasa yace Ki koma ki zauna a inda mutane suke jiran ƴan uwan su marasa lafiya , zan je na dawo ki tabbatar kin ci abinci , kar ki zauna da yunwa ,     Kamar jira take yayi mata umarni ta ɓalle murfin motar ta fita , hankalin ta gaba ɗaya yayi kan falmata , bata damu ba sam da  sauyin yanayin da ta gani tare da shi da damuwar da ta bayyana a gare shi , bare har tayi wani dogon nazari akan hakan ,"       Gyara zaman hijabin ta tayi tare da sake riƙo ledar hannun ta da kyau ,ta kama tafiya ,"cikin ran ta tana aiyana baza ta sha wannan kayan daɗin ba falmata zata ajiyewa tana farkawa ta bata ta ci ta sha !   Tuƙi yake yi akan hanyar sa ta komawar sa gida amma rabin hankalin sa bai tare da shi , yana ga tunanin halin da yarinyar ta tsinci kan ta a ciki , ba zai yiwa kan sa ƙarya ba tun da jimawa ya fahimci ya faɗa tsundum cikin so da ƙaunar yarinyar da ko a mafarki idan aka ce masa shi zai so mace irin ta zai ce ƙarya ne , toh amma tun da ya gagara kaucewa faɗawa a soyayyar ta , sai ya ɗauki hakan a matsayin kaddarar sa ce watakila matar auren sa ce ubangiji ya turo masa ita a haka , dan haka sai ya shiga neman hanyar da zai yi ya gyara ta ta zamto irin macen da shi yake son ta kasance matar aure a gare shi , karatu yake da nufin sa ta a farko bayan ya kai ta gidan su wurin mahaifin sa , tayi karatu mai ɗan zurfi zuwa ko da matakin diploma ne sai ya aure ta , Toh sai kuma ƙwatsam ta ɓace masa , ya sha wahalar neman ta bata nan ! , har ya fara dangana da rashin ta sai kuma ta ɓullo da wani al'amari mai girma a tare da ita ,"ciki ba tare da tayi aure ba , baya tunanin ko uban cikin jikin nata ta san shi ," Al'amarin ba ƙaramin firgita shi yayi ba ya taɓa ran sa fiye da zato , saboda soyayyar gaskiya yake yi mata ," A tun bayan barin ta da yayi yanzu ya kamo hanyar sa yake bincikar kan sa tare da ƙwanƙwasar zuciyar sa ko Allah zai sa ya ji wani sauyi na daga soyayyar da yake mata ta zuwa wani yanayi na ƙi ko kaɗan ne a saboda girman bakon al'amarin da yake tare da ita marar kyau ? Wanda zai yi amfani da hakan wurin yakice ta daga cikin ran sa baki ɗaya ya shafe babin rayuwar ta daga ran sa ? Sai dai ko kusa shi ya gagara ya ji alamun ya tsane ta , a maimakon tsanar sai yake jin wani matsanancin tausayin ta yana sake lulluɓar shi , zuciyar sa tana raya masa FYAƊE aka mata , fin ƙarfi aka gwada mata ba da son ran ta bane , ita ɗin abar a tausayawa ce , abar a tallafa ce a bata kulawa , a tsaretar da rayuwar ta daga faɗawa mummunan yanayi dangane da irin halin da ta tsinci kan ta a ciki a ƙarancin shekarun ta ,"     Sashi mafi rinjaye na zuciyar sa ya ji yana ƙarfafar sa akan Ya tallafe ta , kar ya guje mata , ya zamto gata a gare ta kar ya ƙyamace ta , ya Aure ta ya taya ta riƙo tare da tarbiyyartar da abin da zata haifa HAKAN TAMKAR JAHADI NE a gare shi ,    Da wannan dogon tunanin ya ƙaraso gidan su da yake kan titin danboa road yayi hon maigadi ya buɗe masa kofa , kai tsaye falon mahaifin sa yayi wa tsinke bayan ya ajiye motar sa , kamar yadda ya saba a  zaune ya tarad da shi bisa wheelchair hannun sa riƙe da Alqur'ani mai girma yana ƙarantawa da mabayyanin sauti . Sai da ya ɗan tsimaye shi ya ƙarasa ayar da ya ɗauko ,     Sannan suka gaisa cikin kulawa da nuna tsantsar ƙauna daga mahaifin sa ," ƴan tambayoyi yayi masa game da yanayin aikin sa kasantuwar mahaifin na sa professor ne da ya sha ya ƙoshi ya tumbatsa a harar ilmin kimiyya , yanayin rayuwa ya juyar da lamarin sa haka ya kasance zaune bisa kujerar marasa lafiyar ƙafa bai zuwa ko'ina .      Ji yake batun yakaka yana zungurar sa akan ya faɗawa mahaifin sa , wani sashin ya dakatar da shi da ya bari har ya samu ƙarin bayani daga bakin yarinyar dalla-dallah ta yadda zai ji karfin zuwa da maganar tare da amsa duk wasu tambayoyi da ka iya zo mar daga baban sa !     Dan haka ya miƙe yana mai yin sallama da baban nasa ,     Har ya ɗauki hanyar sashin sa , sai kuma ya dawo ya kutsa kai zuwa ainahin cikin gidan sashin mahaifiyar su da yanzu ƙannen sa ne ke rayuwa a ciki ,      A babban falon ya tarar da su suna harkokin su , ƴan mata ne su uku ya da ƙanwa , babbar cikin su zata yi kimanin shekaru ishirin da biyar sai mai bin ta sai kuma ƙaramar su ,    Har suna rige-rige wurin gaishe da yayan nasu inda shi kuma ya amsa musu da yalwatatciyar fara'a bisa fuskar sa ,'       Girls , so nake ayi girki mai kyau wanda marar lafiya zai ji daɗin ɗanɗanon sa a bakin sa , kamar girki kala biyu haka , a dafa tea da kunu nan da awa biyu zan shigo na ɗauka ,"    Toh company Suka haɗa baki wurin amsa masa tare da barin abun da suke suna nufar hanyar kitchen , ta cikin falon   Ƴar dariya yayi yana girgiza ,"    Nace muku sunan nan ya fita a bakin ku ko ? Ya furta hakan yana mai nufar hanyar barin falon     Har ya fita ,  ya dawo ,"    Zahra ! Ƙaramar su ta amsa gami da dawowa baya ,    Na'am big bro Nace ba ! a cikin kayan ki ki ware kamar kala biyar masu kyau ki ajiye idan na zo ɗaukar abincin marar lafiyar zan haɗa da kayan na kai musu ,     Toh big bro zan ɗauko yanzu , biyar sun isa ko ?   Sun isa!  ya ansa yana barin falon . A duk ranar da ya kwana a asibiti toh yini yake yana bacci idan ya dawo , sallah kaɗai ke tashin sa sai ko cin abinci , kafin zuwan wani daren , saɓanin yau da sam ya gaza yin bacci sai juye juye yake yana kallon agogo , zuciyar sa ta zurfafa wurin son samar masa da mafita , shin daga ta haihu ne  zai aure ta ko kuwa zai bari tayi karatu kamar yadda yake da buri ?? Tunowa yayi bai san matsayin sa ba ma tukun a gurin yarinyar duk wannan tsare-tsaren iska yake , daga ta nuna ƙin amincewa kome ya rushe , ba shiri ya miƙe daga kwanciyar da ya samu kusan awanni biyu yana yi , Karfe ɗaya da mintuna goma agogon ɗakin ya nuna , lokacin sallar azahar ya shigo ,     Kai tsaye ya sake shiga banɗaki ya sakarwa kan sa ruwa tare da sake ɗaura alwala ya fito ,"    Mai ya shafa sama-sama ya buɗe ma'ajiyar kayan sa , ya ɗauko wani shuɗin yadi marar nawi mai haske ya saka , ƴar saisayayyar sumar sa ya taje har zuwa ɗan zagayayyen sajen da ya ajiye a gefe da gefen fuskar sa , ya ɗauko turarukan sa ya fashe jikin sa . Ya zurara bakaken takalman sa yana ɗora igiyar ɓakin agogon hannun sa ,    Ficewa yayi a ƙafa ya nufi babban masallacin da yake bakin titin shigowa unguwar su domin yin sallar azahar . Ƙarfe biyu dai-dai tayi masa a harabar asibitin , kai tsaye ya nufi emergency ward , hannun sa riƙe da ɗan kyakkyawan gwandon roba mai ɗan girma da aka zubo kulolin abinci zuwa ƴan ƙananun flask guda biyu da cups biyu , chokula biyu da plates guda biyu sai serving spoon , ɗayan hannun nasa kuma ya riƙo ɗan ƙaramin akwati , Da gudu security ya taso ya karɓi kayan hannun nasa yana masa sannu da zuwa ," Yana shiga ya tarar da babu gadon falmata , ya tambayi likitan ina yarinyar da take gado mai lamba goma ?    Nan yake sanar da shi ta farka har an mata chanjin ɗaki zuwa cikin ward , dan haka ya nufi ward , security biye da shi . Tun yana shiga ya hango su falmata daga ƙuryar ɗakin gado na ƙarshe , tana kishingiɗe an ɗago mata gadon ta wajen kan ta domin ta ji daɗin kwanciya ," Yakaka tana ɗosane a bakin gadon ta tattara hankalin ta baki ɗaya ga falmata tana shayar da ita hollandia yogurt sannu-sannu , Tana labarta mata irin jimawar sa tayi a sume da taimakon da dakta hamza yayi musu ," Sannu patient ɗina kin tashi ? Ah lalle jiki yayi kyau tunda ga shi har kina shan yogurt , to yaya me kike ji yanzu a jikin ki ? Akwai inda yake miki ciwo ? Da ƴar fara'ar ta ta waigo inda take jin tashin muryar sa , Da sauki dakta , dai-dai wurin raunin kawai shine yake min zogi , sai kuma kaina da yake min ciwo kaɗan-kaɗan , mun gode dakta Allah ya saka da aljanna ," Murmushi ya mata , cikin ran sa yana jin tausayin makantar ta ," Babu kome ɗan pain ɗin da kike ji saboda sabon rauni ne , daga ya ɗan yi kwana biyu zaki daina ji , ciwon kan da kike ji saboda sabon jinin da ya shiga jikin ki ne , zai daina da zarar jikin ki ya dai-dai ta ,' akwai magungunan ɗauke zogin ciwo za'a kawo miki ," ki dunga cin abinci sosai saboda ki samu ƙarfin jiki ," Duban sa ya mayar ga yakaka wacce tun da ya ƙaraso ƙamshin turaren sa ya bigi hancin ta ta ji zuciyar ta ta hautsina , sam ƙamshin bai mata ba , dan haka ta koma daga gefe ta tsaya tana yatsina fuska gaba ɗaya gumi keto mata yake amai yana sasuƙar ta sai dai kuma babu kome a cikin ta idan banda ruwa ," Ga abinci nan ku ci , kiyi wanka ki sauya kayan jikin ki , ga kaya nan na taho miki da shi a cikin nan , Ya mata nuni da kayan da security ya ajiye a gefen gadon ya tafi, " Kai ta gyaɗa kafin ta ce Mun gode Allah ya biya ," cikin ran ta tana Allah-Allah ya tafi saboda warin turaren sa da ke neman kai ta ƙasa , babu abun da take so a yanzu irin ta shaƙi ƙamshin turaren bature kam silum , wanda ta san babu damar hakan domin kayan su yana kulle cikin shagon ", Abuwar mai yadi ," dan haka ta Kai hannun ta biyu ta sa ta rufe rabin fuskar ta daga kan hancin ta zuwa ƙasa ," Ware idanun sa yayi sosai yana kallon ta , yadda ta toshe hanci ya sa shi ɗan shaƙo numfashi ko zai ji inda wari yake tasowa amma shi bai ji ba ," Bai ce kome ba ya juya ya fara tafiya , tare da cewa watakila zan dawo zuwa yamma ," ! Gaskiya kwana biyu ina mutunci kut! 😂 Watau rubutu nake muku babu kakkautawa, duk domin na Baku nishadi. 😍 Da fatan nima zaku bani tukuici , ta hanyar fada min ra'ayoyin ku, / Me kuka tsinkayo zai faru nan gaba? Wai shin bakwa cigiyar biyamuradi YOUSSOUFA ne? ? 😂    [6/24, 10:59 AM] +234 701 013 7848: MAFARI...... ( Hargitsin rayuwa ) umm'muaz 23 Cikin sati guda da suka yi a asibiti sun ga gata tare da kulawa daga wurin doctor hamza , har ma da ƙanwar sa rahima, domin kuwa kusan kullum sai ta zo da yamma ta taho musu da abincin da take girka musu na dare , shi kuma doctor hamza ke zowa da na safen ," da rana kuma ya yo musu take away daga sidic's ,ruwa kan sa na roba suke sha , ga lemuka da kayan shayi irin na garari , biscuits, cake , lokar gadon su cike take taf da cimaka iri-iri , tamkar dai wasu ɗiyan attajirai ,    Rahima tana da matuƙar surutu da wayon tsiya, yarinya ce da kaɗan ta girmewa yakaka , bai wuce shekaru biyu ta bata ba , ita ce ƙarama a ƙannen doctor hamza ," a halin yanzu ta gama secondry sch tana jiran sakamako , " doctor hamza shi yace mata ta dunga zuwa ta na ɗan taya su hira ko da ta awa biyu ce , bayan ya nemi iznin mahaifin su ,  yayi masa bayanin su falmata da ƙudirin sa akan su na taimaka musu, sai dai ya boye masa cikin jikin yakaka na banza ne ,maimakon ya fadi gaskiya sai ya ce masa boko haram ne suka kashe mijin ta tun a garin su ," Maifinsa bai ƙi ya kawo su gidan su zauna ba , sai dai yayi masa gargaɗi mai karfi kamar yadda ya saba yi masa a kullum cewar ,"Ya tsoraci MATA tare da ƙaidin su yayi hankali da lamarin mata domin sau dayawa su ɗin ba'a gane gaskiyar su , wanda duk ya bada gaskiyar sa a gare su tabbas zasu takaita shi watarana ,"        Kamar koyaushe ya amsa masa yana jin yadda wani ɗaci ke yawo a zuciyar sa , sam bai so ba da mahaifiyar su ta zamto silar da ya sa mahaifin su ya samu mummunan tabo akan mace da yakasance kullum kalaman sa masu tsauri ne akan MATA , ********* Yau yake da niyyar kai yakaka ayi mata scan tare da gwaje-gwajen da ya kamata ayi wa mata a tun farkon samuwar cikin su , duk da cewa har kawo yau bai sake tada maganar cikin ga ita yakakar ba wacce ya lura ita bata da wata damuwa da zaman cikin a jikin ta , abun da bai kai ma ga gama fahimta ba kamar son cikin take sosai  , saɓanin sauran matan da ya sani da suke shiga damuwa tare da ƙin abun da yake cikin nasu a duk lokacin da suka samu cikin ta haramtatciyar hanya irin nata , sai dai ya danganta hakan da kasancewar yakaka yarinya ce kuma akwai ƙarancin wayewa da rashin ilmi a tare da ita , ko ma menene shi daman ba shi da burin raba ta da cikin jikin ta wanda ya riga ya fahimci yayi ƙwari a mahaifar ta . Ya zaɓi ya kaita wani asibitin daban a duba ta ne a saboda ƙoƙarin sa na kare martabar ta ko da anan gaba ya aure ta , domin a halin yanzu kowa ya san ba shi da mata , to kuma duk sauran likitocin da zai iya haɗa yakaka da su , abokanen aikin sa ne da suka riga suka san juna sosai ,ya kai ta wurin su a zuwan matsayin me take a gare shi ? Bai son a kodayaushe ya dunga yin ƙarya dan haka ya fi son ya kaucewa duk wani abun da zai sa shi yayi ƙaryar ,"   Sai da ya bari rahima ta zo misalin karfe huɗu da rabi , ta hau sama ofishin sa tare da ajiye masa na shi abincin , nan yake sanar da ita zata Zauna tare da falmata , shi da yakaka zasu je wani waje su dawo ," Tare suka shiga ward ɗin inda suka tarar da su suna ƴar hirar su , babu laifi cikin sati guda falmata ta ji sauki sosai saboda kulawar magunguna masu kyau da take samu zuwa abinci mai inganci , uwa uba kwanciyar hankalin da ta samu , yini take a kan gado iskar fanka tana kaɗa ta , ga ta ga yakakar ta a gefen ta , wanda hakan shi yafi kome sanya ta farin ciki ,      Cikin fara'ar da jin muryar su ya sanya ta take gaishe da doctor hamza da zuwa yanzu take matuƙar girmama shi tare da ganin ƙimar sa har ma take jin sa a matsayin wani jigo cikin rayuwar su ita da yakaka , Shima faram-faram ya amsa mata yana mai sake tambayar ta yanayin jikin nata , kafin ya maida duban sa ga yakaka wacce take zaune bisa kujerar gaban gadon , "suna gaisawa ita da rahima wacce suka yi sabo da juna cikin ƴan kwanakin ," Duban ta ta mayar kan doctor hamza tana mai gaishe shi , cikin ƴar siririyar muryar ta ,    Fuskar sa a sake ya amsa mata yana mai kallon fuskar ta da take fayau babu ko ɗigon kwalliya sai ƴan siraran shunkuran ta "zane" da suke tarwai akan farar fuskar ta ,     Fatima zamu je na kai yayar ki wani wuri baza mu daɗe ba zamu dawo ga rahima nan zata kula da ke kafin dawowar mu kin ji koh?    Toh yaya dakta sai kun dawo ! Yakaka sai kun dawo ! Zo mu tafi ,"   yace da ita yana mai fara taku ,"     Tiris ! tayi akan kujerar , ina kuma za su ? ? Ita fa sam bata son kaɗaicewa da shi , duk ya bi ya ishe ta da kallo ga warin wannan ƙaƙƙarfan turaren nasa da ba so take yi ba ,"     Kallon fuskar rahima tayi wacce ita ma ɗin ita take kallo cikin nazari , dan haka ta miƙe a sanyaye gami da yi musu sallama bayan ta jaddadawa falmata akan yanzu zata dawo ! A motar sa suka fita a asibitin , duk da cewa har zuwa yanzu bai faɗa mata inda zasu ba ," sai da ya hau titi ɗoɗar tukun ya juyo ga kallon sa kan ta da ita kuma ta juya fuskar ta ga kallon titi ,"    Ƴar kwantatciyar sumar da take gefen kunnuwan ta zuwa gaban goshin ta da tayi luf-luf yayi wa kallon daƙiƙai kafin ya maida kallon sa ga titin gami da yin gyaran murya ,"          Asibiti zan kai ki a auna ki tare da duba lafiyar abun da yake cikin ki , dan haka ina son sanin sunan ki mai kyau , domin ayi amfani da shi wurin buɗe miki file ,"      A hankali ta juyo da ganin ta kan shi ,"       Cikin ran ta tana jin daɗin yau karo na farko bayan ita da falmata wani ɗan adam ya nuna kulawar sa akan cikin jikin ta har ma zai kai a duba lafiyar abun da yake cikin , "     Sai dai tambayar sa ta ƙarshe ta bata mamaki daman duk zaman su bai taɓa sanin sunan ta ba ??? Babu shakka ita bata taɓa ji ya kira sunan ta ba , ko magana zai mata kawai yana jefa maganar sa ne a saitin ta kai tsaye ba tare da ya kama sunan ta ba ," amma ai yana ji koyaushe falmata tana kama sunan ta a gaban shi , sai dai idan wani walakanci ne hakan ," zai ce bai san sunan ta ba .    Kamar ya san tunanin da take    Ba tare da ya dube ta ba yace ,"    Sunan ki mai kyau nace ,"wannan sunan da ake kiran ki da shi ba suna mai kyau bane dole akwai ainahin sunan ki ,    Bani da wani suna bayan wanda ake kira na da shi ,"    Ta bashi amsa ƙasa-ƙasa , a ran ta  Kuwa tana jin haushin kalmomin sa ya za'a yi yace sunan ta bashi da kyau ??   Ba wanda ya sake cewa ƙala har suka ƙaraso ɗan ƙawatatcen asibitin mai zaman kan sa da yake cikin unguwar G.R.A , Jerowa suka yi suna tafe tamkar sabbin ma'aurata , ta wutsiyar ido ya kalle ta tana sanye ne da wata atamfa ruwan ɗorawa da aka yiwa dinkin doguwar riga wacce ta buɗe daga ƙasa ,  ɗaya daga cikin kayan da rahima ta ba su ne ," nan ya ga yadda ɗankwalin kan ta yayi baya sosai har ya bayyana lallausar sumar da take gaban kan ta , gyalen ta da ta rufu da shi daga kafaɗar ta iskar juyin yanayi da ake na ta kaɗa shi ,"       gani yayi ta yi masa kyau ba kaɗan ba ," Sam baza'a ce mace mai ciki bace , domin idan ban da cikar da ta sake yi tayi ƴar ƙiba kaɗan tare da ƙarin haske , babu wani alamun ciki , cikin bai bayyana a sarari ba ,"             Ki gyara ɗan kwalin ki , kuma ki rufa gyalen zuwa kan ki ,"    Ta tsinkayi muryar shi yana bata umarni ," ba tare da ta ce uffan ba tayi yadda yace lokacin da suke ƙarasawa cikin ainahin asibitin , Ba tare da ɗaukar lokaci ba ya shige gaba ya kammala kome da ake yi a dokar asibitin kafin a ga likita , wanda kuɗaɗe ne tsababa saboda asibitin na manya ne ,   Wurin bada sunan ta ne ya so shiga ruɗani kafin lokacin da zuciyar sa ta yanke masa shawarar abun da ya kamata  ," Aka yi musu jagora zuwa wajen ainahin babban likitan mata da yakasance shine mamallakin asibitin baki ɗaya ,"   Nan ya tare su da fara'a duk da cewa ba wai ya san doctor hamza bane amma yanayin sa ya bayyana masa wayewar sa tare da ilmin da ya hango tare da shi , "       Bayan bayanin da doctor hamza yayi masa akan a duba lafiyar uwar da abun da yake cikin ta tare da son sanin ranar da zata iya kasancewa ranar haihuwar ta ,"    Likitan ya fara aikin sa cikin gwanancewa, nan ya fara da ɗaukar jinin ta domin yin gwaje gwaje , ya kuma bata wata ƴar roba yace ta kawo fitsarin ta tare da ƙiran ɗaya daga cikin nurses akan ta gwada mata banɗaki  , bayan ta dawo yayi mata awun blood pressure,  ya ga jinin ta dai-dai ne , sai yayi umarni da ta hau wani ɗan gadon duba marasa lafiya da yake gefe guda cikin ofishin domin yayi mata scanning ," Da jaan ƙafa ta ƙarasa bakin gadon ta hau ta zauna ,"    Kallon ta likitan yayi lokacin da yake jona na'urar da jikin babban tv da yake kafe a gefe ,"     Amarya gyarawa zaki yi ki kwanta mai kyau ki miƙe kafafun ki ,"    A ɗarare tayi yadda ya umarce ta tana mai sake gyara rigar jikin ta da kyau ,"    Da ido doctor ya yi wa hamza alama akan ya mata bayani yadda zata gane ,"        Ki ɗaga rigar ki , ki buɗe cikin ki hoton jariri za'a yi ta haka za'a gane lafiyar sa ," ya furta hakan yana mai maida ganin sa ga fuskar wayar sa ,"    Hoton jariri?? Ai kuwa zata so ta ga hoton abun da yake cikin nata ," wataƙila yayi kama sosai da baban sa ? ," tuno da hakan da tayi ya sa wani siririn murmushi ya bayyana kan fuskar ta ,    ta tashi tsaye ta tattara doguwar rigar ta , dogon wondon da ta sa ta ciki ya bayyana ,"      Cikin nutsuwa ya fara mata scanning ɗin , yayin da shi da dakta hamza suka maida hankalin su baki ɗaya ga fuskar tv lokacin da ƴar jaririyar da take cikin mahaifiyar ta ta bayyana tana ta hidimar ta hankali kwance,  a yau tana da sati goma sha tara da kwanaki biyar , "komen ta yana lafiya ƙalau a yanayin da ya dace ,hasashen ranar haihuwar ta ya nuna biyar ga watan goma ," nan da watanni huɗu da ƴan kwanaki kenan ,"       Wow what a beautiful busy baby girl , ? See those wee fingers are very close to the mouth,!     Doctor ya karasa zancen da ƴar dariya a fuskar sa yana mai maida duban sa ga fuskar doctor hamza ,"wanda shima ya ga wutsilliyar da ƴar jaririyar take da hannuwan ta,"wani abu yaji ya taɓa ran sa , fuskar sa kadaran-kadahan yace ,"    Yeah the baby looking super comfy and growing perfectly , ya furta hakan yana mai jefa kallon sa ga yakaka wacce ko kalma guda bata gane ba cikin ƴar gajeruwar mahawar da suka yi , sai faman raba ido take tana daga kwance , Congratulations once again Mr and Mrs Hamza Mustapha Dilmari Likitan ya furta haka tare da miƙawa doctor hamza hannu suka yi musabaha , dai-dai lokacin da suka tashi domin tafiya , bayan da likitan ya kammala shigar da duk wasu bayanan da ya tattara akan yakaka da abun da yaje cikin ta zuwa cikin computer Ya aika da shi ainahin wurin wanda zasu cigaba da yi mata anti-natal , bayan ya duba duk wasu gwaje-gwajen da ya yi mata , yaga bata tare da wata babbar matsala ,"  nan ya miƙa musu takaddar magungunan da ya kamata ta dunga sha tare da wani ɗan kati wanda da shi zata dunga amfani wurin zuwa awo ,"     Har sun yi taku biyu , yakaka ta tsaya tare da juyowa ta fuskanci likitan , bayan ta sauke idanun ta ƙasa tace ,"      Likita toh ina hoton jaririn da ka ɗauka ?            Ta furta hakan tana mai jin ƙwalla na cika idanun ta domin ta so ƙwarai ta ga jaririn , sai kuma ta ga har zasu tafi bata ga hoton na sa ba ,    Tiris likitan yayi yana duban ta , domin shi a idanun sa bai ga alamun ƙyauyanci har haka a tare da ita ba ,    Wani takaici ne ya rufe hamza , shi dai gidadancin yakaka na ci masa tuwo a ƙwarya ,"          Lokacin da ake hoton ina hankalin ki yake ?? Wuce mu tafi gaba idan mun sake zuwa kya ga hoton , ya furta hakan yana mai kokarin danne ɓacin ran sa akan tsantsar son cikin da yake hangowa cikin idanun yakaka ,      Waye uban cikin ?tabbas yawan soyayyar ɗa wurin uwar sa tana da alaƙa da son da take yiwa mahaifin sa ,"    Bayan sun kama hanyar komawa gida yakaka ta katse shirun da suka yi da faɗin ,"    Inaso na je bakin kasuwa na ɗauko kayan mu da suke shagon da muke kwana a bakin sa ,"     Shiru ya yi kamar ba zai amsa ba saboda zuciyar sa da take ta kai kawo akan son sanin ko yarinyar tana da wata alaƙa da uban cikin jikin ta ,?  ko zaton sa ba gaskiya bane , ? ko dai da amincewar ta ta bada kan ta ga wani ƙato ??      Babu buƙatar ki ɗauko kayan , ki bar su kawai zan saya muku wasu nan gaba !      Ta bar kayan ? Yana nufin rabuwar ta da duk wani abu da ya shafi bature kam silum ɗin ta ,!' bata jin zata iya ,'domin kome da ya shafe sa abun so da ƙauna ne a wurin ta , baya ga haka kuma ba ƙaramin taimakawa  suke wurin ɗebe mata kewar sa da ke cin zuciyar ta a kullum ba ,   Ni dai Dan Allah ka kai ni na ɗauko , akwai abu masu muhimmanci a cikin jaka ta,"     Duban sa ya mayar kan ta   Abu masu muhimanci , meye su ? Agogon sa da hoton sa ta amsa masa kai tsaye babu ƙunbiya-ƙunbiya ,!    Gangarawa yayi gefen titi ya tsaya , tare da maida hankalin sa baki ɗaya kan ta ,"     Agogo da hoton wa ??   Ya jefa mata tambayar yana mai tsare ta da idanu ,"    Ɗago da kan ta tayi tana kallon tsakiyar idanun sa , ƙwarai yayi mata kwarjini kuma tun farko shi ɗin bai taɓa zuwa mata da sigar wasa ba , uwa uba zuwa yanzu ta san cewa abun da suka aikata da bature kam silum har ta kai ga samun ciki ba abu ne mai kyau ba , dan haka ya zama dole ta koyi boye ainahin yadda kome ya faru da dangantakar ta da shi ,"    Da inda-inda tace masa Hoton baa-baban mu ne da agogon sa ,     Tsai yayi yana kallon cikin ƙwarar idanun ta a koƙarin sa na son gano gaskiyar ta ,"    Dan Allah ka kai ni Ta sake yi masa magiya tana marairaicewa,"    Ɗauke kan sa yayi tare da tada motar , sashi guda na ran sa na tabbatar masa da bata da wayo da wayewar kan da zata iya masa ƙarya , sam alamun ta bai yi kama da na wacce zata iya lanƙwasa zance ta sauya masa launi ba ," A dai-dai ƙofar shagon ya tsaida motar ƙarkashin umarnin ta da tace masa nan ne shagon ," Ba ƙaramin farin ciki abuwar mai shago yayi ba da ganin yakaka cikin ƙoshin lafiya , ya ɗora da tambayar ta falmata , domin labari ya isar masa na abun da ya same ta , ya kuma ga shaidar jini a bakin shagon sa washegarin ranar da abun ya faru , Ya shiga dumuwa sosai ta yadda yake ganin har da rashin taimakawar sa ya sa suka afkama masifa ," ga yadda suka samu labari falmata ta riga ta mutu , hakan ne ma ya sa bai ko je neman su asibiti ba ," Bayan gaisuwa tare da jajantawa yakaka ta buƙaci ya bata jakar baccon su , nan kuwa ya fiddo mata da su , suna nan yadda suka bar su , " a cewar sa yayi niyyar cigaba da ajiyer su domin ya san zata dawo ɗauka , nan dai suka rabu suna mutunta juna ,!    Daga yanzu baza ku sake dawowa bakin kasuwa da sunan zaman kan ku ba ," idan ƙanwar ki ta samu sauƙi zan tafi da ku gidan mu ku zauna tare da su rahima , har zuwa ....       sai kuma yayi shiru gami da juyowa ya dube ta , ta nutsu tana saurarar sa ,"     maida duban sa yayi ga tukin kafin ya jefa mata tambaya     ko baza ku bini gidan mu ?    da sauri ta ɗago kan ta , ita kuwa da daman kullum da tunanin inda zasu samu mafaka bayan barin su asibitin take kwana take tashi ,Ta yaya zata ce baza su bi sa ba ? To ina zasu da ya wuce inda zai kai su ?? Babu !      zamu bika yaya dakta , kuma mun gode Allah ya saka da alheri ya baka abun da kake so duniya da lahira , yadda ka taimaka mana kai ma Allah ya ɗaukaka ka ,!   sosai kalaman ta suka burge shi tare da dadaɗa masa rai , a yadda yake mata ganin bagidajiya bai taɓa zaton ta iya kalamai masu nutsuwa haka ba ,"    da murmushi a fuskar sa ya amsa a bayyane da ,           Ameen Nurii . Bayan sati biyu Falmata ta warke ras kamar ba ita ake sallama daga gadon asibiti a yau ɗin ba , tayi ƴar ƙiba mul-mul , fatar ta mai ɗan haske ta sake washewa , fes da ita cikin jar doguwar rigar da yaya dakta ya saya mata , kafafun ta sanye cikin sabon farin silafa ɗan madina , ta ɗora ɗan bakin hijabi akan ta ," Duk wani abun da ake kafin a ba wa mutum sallama daga gadon asibiti doctor hamza ya gama yi inda likitocin ta suka buƙaci ta dawo bayan sati shidda su sake duba ta , "  Rahima ita ta taya su suka harhaɗa ƴan kayan su domin tafiya da su gida , sai dai da zuwan doctor hamza yace duk su bada bokitaye zuwa buta tabarma da sauran tarkacen kayan ciye-ciyen da basu riga sun cinye ba ga marasa lafiyan da ba'a riga an sallame su ba masu ƙaramin ƙarfi , daga su sai ɗan ƙaramin akwatin da rahima ta basu wanda suka juye duk ƴan kayan su a ciki suka fito ," zuwa jikin motar sa da yace su tsumaye shi a wurin , bai ɗauki lokaci ba yazo ya buɗe motar yayi musu iznin shiga , yakaka da falmata suna mazaunin baya yayin da ƙanwar sa take daga gefen sa , sannan ya tada motar suna masu barin harabar asibitin ," Kai tsaye ya wuce da su shagon telan da yake yiwa rahima ɗinkunan ta da shi doctor hamza ya saya atamfofi , yadiddika da ƴan lesuka , ya bata yace ta kaiwa telan ta ya ɗinkewa su yakaka , kowaccen su shiga takwas-takwas ,"      Telan ne ya buƙaci a kawo su ya gwada su domin gujewa kuskure ," Da rahima ya haɗa su yace su shiga a gwada su , ya kuma faɗa musu ranar da za'a zo ɗaukar ɗinki saboda ya riga ya biya sa kuɗin ɗinkin baki ɗaya ! Har sun fara taku ya kira ta        Rahima ki sake jaddadawa tailor kar fa yayi musu ƙaramin ɗinki , ita babbar ma kawai duk yayi mata dogayen riguna buɗaɗɗu ,"      Toh ! ta amsa masa Ba'a ɗauki lokaci ba suka fito daga shagon , rahima sai faman dariya take tana tsokanar falmata ,"      Fatima da kuɗi goggagun mata suke zuwa a maida musu fasalin jikin su irin naki , kin gan ki kuwa kamar wata "Kim Kardashian "ta ƙarasa zancen da dariya ,' Da murmushi akan fuskar su suka haɗa baki wurin tambayar ta wacece kuma , "kimkadarshia"???      Wata celeb ce Ta amsa musu Tana ƙara ƙarfin dariyar ta jin yadda suka kira sunan a hargitse," Yana daga cikin motar yake hango fararen haƙoran ta tana darawa , tsawon ta da takun kafar ta yana daga cikin abun da yake daɗa jaan hankalin sa akan ta , duk da cewa yanzu da cikin ya shige watan sa na biyar ya fara bayyanuwa da ya sa tafiyar ta ta tafara sauyawa zuwa irin ta mata masu ciki ,    Shima tsintar kan sa yayi yana mai murmusawa a saboda ganin fara'ar ta , ƙwarai ya fuskance ta ita ma'abociyar murmushi da haƙora ce , kusan koyaushe fuskar ta da haskakken murmushi ƙwarsi ta dace da sunan da zuciyar sa ta raɗa mata watau nurii . Daga nan hanyar gida ya ɗauka , suna isa suka fiffito daga motar , inda yakaka take bin illahirin gidan da kallon baƙunta ,    Ku zo muje ku fara gaishe da Baban mu ,    Suka tsinakayi muryar sa bayan ya kulle motar "    Shi ya shige gaba suka doshi kyakkyawan ginin da yake tsaye a saitin su , a bakin kofar ya ce su tsaya ya shiga ya sanar da shi tukun ,"    Nan suka tsaya duk su ukun har da rahima ,"     Bai jima ba yayi musu iznin su shigo yana daga ciki,'     Tsayawa suka yi daga baya har sai da rahima ta fara shiga sannan suka bi bayan ta hannuwan su a sarƙe ,"     Babban falo ne tafkeke , dan haka suna shiga taku biyu suka yi yakaka ta ɗurƙusa bisa kafet ɗin da yake malale a ɗakin tana mai fuskantar sa fahimtar hakan da falmata tayi ya sa ita ma ta zube guiwar ta a ƙasa , suna masu gaishe shi ,"        Da murmushi a fuskar sa yace   Ku shigo , ku shigo , kar ku tsaya daga chan ku zo daga nan , "  ya musu nuni da kusa da shi a ƙasa inda rahima ta zauna ,"     Tasowa suka yi suka dawo inda ya nuna musu ," sannan suka sake gaishe sa kan su a sunkuye ,"    Ya amsa musu fuskar sa a sake yana mai musu kallon tsanaki ,"   Daga wanne gari kuke ? Ya tambaye su ,"     Mairambiri ," yakaka ta amsa masa ,    Mairambiri , ya maimaita tamkar yana nazarin sunan ,! Ina iyayen ku ? Nan yakaka ta bashi takaitatcen tarihin rayuwar su ,"   Ya tausaya musu sosai ,"   A ƙarshe yace su saki jikin su , insha Allah zai kula da rayuwar su gwargwadon ikon da Allah ya bashi ,  muddin suka tsaya akan gaskiya ɗa ai na kowa ne ,!    Daga haka ya basu umarnin tafiya ! Ɗakin da yake gefen na rahima wanda a da yake rufe babu kome cikin sa sai shimfiɗar kafet , nan doctor hamza ya gyara musu , aka sa musu labule da katifu madaidaita biyu , sai ƙaton wardrobe mai kofa shidda , sai fanka da bulb, akwai banɗaki a ciki ,  babu laifi ɗakin yayi kyau musamman a wurin su yakaka da basu taɓa shiga ɗakin da ya kai haka sun kwana ba tun da suke , dan haka su yau ran su fes zasu yi kwanan ƙarƙashin fanka bisa lallausar sabuwar katifar da ta ji sababbin shimfiɗu har da tausasan matasai ,! Biyamuradi youssouf ne a tsaye kan ɗan wani dutse , waya ce a hannun sa yana ta faman neman layin hajiya umma fiye da mintoci ashirin amma ya gagara samun ta , yau kwanaki biyu kenan rabon da su gaisa da gida , ya san duk inda take yanzu hankalin ta yana gare shi , Duk da ta san cewa a yanayin aikin su akwai haka , wani lokaci su kan rasa samun layin wayar sa muddin anka tura shi wurin da yake da matsalar hanyoyin sadarwa , kamar dai yadda ya fatu a yanzu , wajen da aka matso da su sam babu kyaun hanyar sadarwa , saboda ya sake nesa sosai da cikin gari , cikin surƙuƙin daji ne da yake gaf da bakin bodar da ta raba tsakanin niger da nigeria , babu mahalukin da ya isa ya san da mutane a gurin sai fa jami'an tsaro ƴan uwan su ,"      Motsin da yaji daga ƙasan ɗan dutsen da yake tsaye bisan sa wanda ruwa yake ɓulɓula ta tsakanin sa ya sanya shi ɗan rankwafawa ya leƙa ,zuwa ɗan kwarin da ruwan ke bi , da yake lulluɓe da bishiyoyi da Koren tsirrai shar , nan ya hango wata barewa tana tsaye akan ƴar ta wacce alamu ya nuna yanzu ta haife ta , domin sai faman lashe ƴar take tana ƙoƙarin ɗago ta ta tsaya bisa kafafun ta , Mafarkin da yake yi a jere kwanaki biyu mai yanayin kama da halin da yaga barewar nan ciki shine ya dawo cikin tunanin sa ," Kwanaki biyu kenan a jere yake mafarki da wata barewa tare da ƙaramar ƴar ta , maharba sun biyo su , sai faman gudu suke a sanadin haka ya sa uwar ta faɗa a rami ƴar kuma ta wuce da matsanancin gudun da ya wuce na ƴar jaririyar barewa kamar ta ," gaban sa ƴar kyakyawar barewar take zuwa ta tsaya , shi kuma ya sunkuya ya ɗauke ta zuwa jikin sa tare da juyawa ya fara gudu da ita maharban na sake bin sa a ƙokarin su na son ganin sun karɓe ƴar barewar daga hannun sa ,' ! Tsumu yayi ya tsirawa barewar idanu ," yana son samun fassarar mafarkin sa ,  Ƙarar wayar sa ita ta jaa hankalin sa ga barin kallon barewar ya maida duban sa ga fuskar wayar da fatan ganin ƙiran daga hajiya umma ne ,"   Sunan tafeeda ne ke yawo bisa fuskar wayar , da ƴar fara'a bisa fuskar sa ya kara wayar a kunnen sa Gaisuwa suka yi irin ta aminan junan da suke tsantsar ƙaunar junan su , daga nan suka ɗora hirar su akan lamuran da suka shafi aikin su ,"   Biyamuradi youssouf ke tambayar tafeedah , yaya yaga number sa ta nijer ce maimakon ta sudan ?saboda shi ma watanni biyu da suka wuce an tura su sudan akan aiki ,"    Ya bashi amsa da cewar ya gama satittikan da aka tura sa ya yi , har wani ya amshi bakin aikin sa ," Nan Biyamuradi youssouf ya tambayi lafiyar mutanen fada baki ɗaya a ƙarshe ya nemi da tafeedah ya haɗa shi da hajiya umma su gaisa idan ya shiga gidan saboda ya gagara samun ta a waya kwana biyu ," Ya ce masa shi ma tun jiya yake gwada layukan na youssouf dakyar ya samu nasarar samun sa a yanzu ,   Nan suka tsaya akan zai tafi fada ya kira shi ya haɗa su da hajiya umma , idan kuma har bai same shi ba zai isar da saƙon gaisuwar sa gare ta tare da mai martaba baki ɗaƴa ," Har sun yi sallama ya sake tsinkayo muryar tafeedah inda yake cewa ,"    Da farko nayi niyyar nai maka bazzata tou amma na gaza hakurewa , watanni biyu masu zouwa , zan shigo nigeria bikin iliyas wanda za'a yi cikin babban birnin nigeria abuja ," Da murna youssof yake bayyana farin cikin sa , ya san iliyas abokin aikin tafeedah ne da suka taɓa aiki tare a magadishu , asalin sa ɗan nigeria ne , da yakasance babban sojin sama , " Shi ma zai so halartar bikin iliyas ɗin kwarai da gaske , tare da farin cikin haɗuwar da zasu yi da aminin sa wanda suka kwashe kusan watanni bakwai basa tare ,"   Sauke wayar yayi daga kunnen sa bayan sun yi sallama da tafeedah , bai sake bi ta kan barewar nan ba ya kaɗa kan sa ya bar wurin ," Assalamu Alaykum masoya ,!    Nasan kun yi jira cikin satin nan , da zaton samun update da wuri , nima na so na baku da wuri , yanayin ne bai dai-daita agare ni ba ! Da fatan kun min afouwa ?    Nagode !                [6/24, 10:59 AM] +234 701 013 7848: MAFARI   ( Hargitsin Rayuwa ) umm'muaz 24 Kwanakin da suka biyo bayan zaman Su yakaka a gidan su doctor hamza , kwanaki ne mafiya jin daɗi da walwala agare su a bakiɗayan rayuwar su ,sun gyagije sun yi fes da su tamkar da ɗai basu taɓa shan wata wahalar rayuwa ba , Doctor hamza yayi bajinta sosai ta yadda ya ɗau nawin duk wasu lamuran su na yau da kullum babu gajiyawa babu ƙorafi ko tozarci irin na wasu mutanen, a gefe kuma ya gama shirin sa na sanya su a makarantu , inda ita yakaka yayi mata rajista da wata makarantar matan aure ta jeka/ka dawo boko zallah , zata fara zuwa bayan ta haihu , Falmata kuma yana fafutukar nema mata wata makarantar makafi mai zaman kan ta , wanda su a shekara mutane 70 kachal suke ɗauka , yana sa ran za'a samu gurbin sanya falmata , ' Amma a halin yanzu su duk biyun ya ɗauka musu wasu malamai biyu mata   ɗayar tana zuwa da rana kamar karfe sha biyu bayan ta taso daga makarantar islamiyyar da take koyarwa , sai ta zo ta koyar da su karatun addini , zuwa karfe biyun rana , wacce take koyar da su boko kuma zata iso karfe huɗu na yamma zuwa karfe shidda take tafiya , ita falmata kome da baki ake koya mata tana saurara a halin yanzu tun da ba makarantar su ta makafi aka kai ta ba , yayin da ita kuma yakaka ake koya mata har da rubutu , Kuma babu laifi ƙwarai suna da saurin fahimta musamman ma falmata , ba'a maimaita mata karatu , daga an fadi ta haddace sa kenan,  ga ta da baiwar harce iya fidda lafuza Sam bata da tsamin baki, "hakan ba ƙaramin farantawa doctor hamza yake ba , da alama yaran baza'a sha wahalar sauya musu rayuwa ba ! Ta ɓangaren ƙannan sa ma basu da wata matsala , zainab da hafsa sune manya kuma sun girme musu sosai zainab tana da ishirin da biyar hafsa tana da ishirin da uku ,dan haka tsakanin su da su yakaka gaisuwa ce kawai bayan haka ko kula sabgar su basa yi , basu ma cika zaman gidan ba domin a halin yanzu ma shirye shiryen bikin zainab ɗin ake nan da sati uku inda zata auri wani babban sojin sama , ita kuwa hafsa boko yayi zafi domin yanzu ne take matakin ƙarshe a jami'a ga kuma taya ƴar uwar ta shirye shiryen biki da suke , tunda ba uwa bace da su a kusa , kusan su biyun suke duk wasu tsare-tsaren su na ƴan mata , sai kuma ƙannen mahaifin su uku mata da su kuma suke gudanar da sauran lamuran da yakamata iyaye mata suyi ," dan haka daga su sai rahima da ta zama ƙawar su su duka biyun suke gudanar da lamuran su , domin ta biye musu sosai tana kwasar duk wasu gidancin su da ƙauyencin su da suke yi sumfuri-sumfuri kuma dai-dai gwargodo tana iyakar yin ta wurin wayar musu da kai a duk lokacin da suka yi wata katoɓarar .    A halin yanzu sun samu kusan watanni biyu kenan a gidan , Kamar kullum bayan dawowar sa daga aikin sa da ya wuni yana yi , ya shigo bangaren sa bayan ya baro bangaren baba inda ya daɗe suna tattaunawa mafi yawa muhawarar ta su akan sha'anin auren zainab ɗin ne , suna tsare-tsaren yadda kome zai tafi cikin tsari mai kyau , sai kuma  a ƙarshe kamar koyaushe idan suka yi zama irin wannan sai hamza ya shigo da batun mahaifiyar su ko da a fakaice ne , a yau ma nema yayi da mahaifin nasu ya amince a sanyo ta cikin lamuran bikin zainab ɗin kasancewar ta babbar ɗiyar ta mace da a karon farko za'a aurar , a wannan lokacin fiye da lokutan baya ya ga bacin ran baban su , inda ya rufe ido yayi ta faɗa a ƙarshe yace kar hamza ya sake sako mahaifiyar su cikin lamuran bikin zainab , shine mahaifin su shi Allah ya ɗorawa alhakin aurar da ƴaƴan sa , ba wata chan daban ba wacce ta zaɓi rayuwar kororo akan zaman aure ," Idanun sa taf da hawaye ya baro sashin yana jin zuciyar sa na ƙara bunƙasa girman laifin ta , Kai tsaye banɗaki ya shiga yayi wanka gami da ɗauro alwalar sallar magariba da ta gabato , ya zira jallabiyar sa tare da sanya ɗan silifa ya rufe sashin nasa ya nufi cikin gidan ,"  hannun sa riƙe da wata ledar da ya biya ya ɗauko a mota mai tambarin "down town" , tare da wata bakar leda . A zaune ya tadda su , suna sake biya karatun su da malamar su ta boko ta yi musu yanzu ta tafi ,' Rahima na yi musu gyaran ƴan ƙananun kalmomin english da ma'anonin su da aka fara koya musu bayan sun gama haddace Alphabet ,"..   Cikin idanun yakaka ya fara jefa kallon sa,  lokacin da ya ƙaraso cikin falon ,    Da sauri rahima ta miƙe gami da karɓar ledar hannun sa suna masu haɗa baki su ukun wurin yi masa barka da zuwa tare da gaishe shi ,"   Yana daga tsaye yana ɗaura agogon da ya zaro daga aljihun wandan sa yake amsa gaisuwar su , "          Da fatan suna muku karatun yadda kuke ganewa ?    Ya tambaye su yana mai nacewa kallon fuskar ta ,   A tare suka haɗa baki su biyun wurin amsa masa ,"    Muna ganewa sosai yaya dakta ," Toh madallah a cigaba da dagewa ,"babu dai wata matsala ko ? Babu matsalar kome yaya mungode,! Daga haka ya fice jin an fara kiran sallah , Da zumiɗin su suka buɗe ledar da ya kawo musu duk da sun riga sun san abunda yake ciki , ilai kuwa shawarma ce naɗi biyar , kowaccen su ta ɗau ɗaya suna murna, ɗaya ledar kuwa agwaluma ce manya-manya nunannu har cikin ledar , ai kuwa yakaka tana ganin agwalumar ta ajiye ƙunshin shawarmar ta gami da sunkutar ledar agwalumar baki ɗaya ,     da sauri ta yunƙura tana tura cikin ta wanda zuwa yanzu har ya shige watanni shidda , kitchen ta je ta wanko musu , ta miƙawa rahima da tace zata sanya musu a firiji ta ɗan yi sanyi kafin su idar da sallah , Bai shigo gidan ba sai bayan sallar isha'i , kamar yadda yake ka'idar sa idan ya shiga masallaci sallar magariba bai fitowa sai yayi isha'i muddin ba wani aiki ne mai girma a gaban sa ba , zama yake yayi ta karatun Alqur'ani . Rahima , yakaka da hafsa ya tarar suna zaune a ainahin babban falon suna hira tare da kallon wani shirin larabawa da ake nunawa a tv , hannun kowaccen su riƙe da agwalumar tana shaa , Da murmushi a kan fuskokin su suka masa sannu da shigowa , hafsa ta miƙe ta shiga kitchen ta fito hannun ta riƙe da babban faranti wanda aka jera kuloli bisa ,      Miƙa masa tayi ,ya karɓa tare da maida ganin sa sashin da yakaka take zaune ,"     Ki shirya gobe ne ranar komawar ki asibiti su duba ki , da safe zan kai ki saboda ina da aikin safe ," Charaf hafsa ta karɓi zance ,"    Big bro kayi tafiyar ka kawai aikin ni zan kaita , ko ba Galaxy hospital ba?       Nan ne , amma nafi son na kaita da kaina saboda akwai wata matsala da muke kan tattaunata da likitan ta ,"     Ki ƙira min zainab ku zo sashi na tare inason yin magana da ku ,!     Daga haka ya juya yana barin wurin ,    Ya bar hafsa nan tsaye da tarin wasi-wasin da take yi akan alaƙar yayan su da wannan ƴar gudun hijirar , kulawar da ta lura yana bata yayi yawa ya wuce na taimako ," meye a tsakanin su ? Tasan yayan su kamili ne kuma managarci bata zargin zai aikata wani mummunan abu , tunanin ta yafi karkata akan wani yanayi da take hangowa a kan fuskar sa a duk lokacin da ya ga yarinyar da kuma tsantsar kulawar da yake mata duk a sunan taimako ," ko ma menene a sannu zata kai ga fahimta fatan ta Allah ya sa ba abun da take zato bane , ," Cikin sati biyun da suka biyo baya shiri ake gadan-gadan na bikin zainab shi da kan sa hamza bai zauna ba , shirye shirye suke ka'in da na'in kasantuwar wannan ne biki na farko da za'a yi a gidan nasu , ƴan uwan su na nesa nesa duk sun fara isowa , haka ma wasu ƙawayen zainab ɗin sun fara sintiri ganin cewa an shigo satin fara bikin sam ƙafa bata ɗaukewa a gidan  , ƴan aiki huɗu mata doctor hamza ya kawo amma duk da haka aiki da aike chakuɗe musu yake ,' Yakaka da Falmata duk a takure suke , ko falon basu cika son fitowa ba suna ƙunshe cikin ɗaki sai fa idan rahima ta tuno su tazo ta ishe su da surutu tare da mitar meyasa basa son fitowa cikin jama'a ," ??    Yau ya rage saura kwanaki uku ayi ɗaurin aure kuma a yau ne za'a fara gabatar da shagulgulan bikin , inda a yau ɗin ne suke shirin yin arabs day dan haka gidan danƙam yake da ƴan mata kawayen ita amaryar da yawancin su daga nesa suke , sun yi guzurin manyan jakankunan su da suke cike da suturun su zuwa kayan kwalliyar su da takalma , dukkanin su gogaggu ne kuma wayayyu , kuma ƴaƴan manya irin ta, yawan su ya sa ɗakin ta ya gaza ɗaukar su , dan haka suka rarrabu wasun su suka samu wuri a ɗakin hafsa , da rahima , sauran ukun kuma suka sauƙa a ɗakin su yakaka , Tashin farko lokacin da suka shiga ɗakin da suka ga su yakaka , ɗaya daga cikin su ta tambayi zainab ɗin da ta rako su ɗakin da kan ta     Friend Waɗannan ɗin su waye ? Ƴan gudun hijira ne ,' ta basu amsa kai tsaye     Yakaka ga ƙawaye na dallah ku ɗan ara musu shimfiɗun ku kafin .....   Tun kafin ta ƙarasa babbar ƙawar ta da tun da suka shigo ɗakin take yatsina tana ƙarewa ɗakin kallo , tace      Zee mekike nufi ? Kaddai kice min kan shimfiɗar da ƴan gudun hijira suka gama birgima zamu kwanta ? Kalan mu ɗauki wata cutar ,? Ko kuwa kwarkwata ta maƙale mana ko amosani ?    Wata ƴar iskar dariya suka kwashe da shi ,"kai sofi baki da kyau ,kuma fa da gaskiyar ki ,"    Ɗan murmushin ƴake zainab tayi   Kai haba dai sofi , baki ga sun waye bane ? Ai kin ga babu alamun ƙazanta har haka tattare da su ," amma bari na samo sabbbin bedsheets idan ya so sai ayi sauya muku, sai su kuma su koma falo suna kwanciya kawai haka yayi ko ? Ta furta hakan tana mai barin ɗakin cikin sauri domun ta kawo bedsheets ɗin , har tayi nisa ta tsinkayi muryar ɗayar su tana cewa ,"    Ki zo da germs kill/anti bacteria dan a wanke bathroom ma sosai  da kuma room freshener ,"    Ta amsa da toh ,"tana ƙara sauri . Sai kuwa ga ta da duk abubuwan da suka lissafa ,'    Su kuma har lokacin suna tsaye akan kafafun su , suna hirararrakin su tare da latse-latsen waya ,      Nan ta zube kayan a gefe , To wa zai gyara ɗakin ina housemaid ?   Cikin ƙosawa zainab tace duk basu nan sun tafi kasuwa ," Duban ta ta mayar kan su yakaka da suke zaune daga gefen wardrobe sun yi shiru kamar ruwa ya cisu , duk suna jin maganganun su ,"     Ke fatima tashi ki je ki wanke musu bathroom ke kuma yakaka ki sauya bedsheets ɗin tare da share musu ɗakin ya fita da kyau ki fesa turaren nan , " ta mayar da duban ta kan ƙawayen ta , muje ɗaki na kafin su gama aikin sai ku zo ku shirya , "   Daga haka suka kama barin ɗakin suna masu cigaba da dararrakin su ,"   Ɗan shiru ne ya ratsa ɗakin , kamar haɗin baki kowaccen su ta ce    Bari ni zan yi aikin yakaka ke baki da lafiya ,'   Bari ni nayi duk aiyukan falmata ke ki zauna anan ki jirani ,"   Nan suka kama musu ƙarshe a dole falmata ta sakarwa yakaka dukkanin aiyukan ganin har ran ta ya fara ɓaci ,"   Bata ɗau lokaci ba ta gama , zuwa tayi ta kama hannun falmatan zo muje mu faɗa musu mun gama sai mu samu wurin zama ko ta waje ne mu zauna ,"     Sama-sama zainab ɗin ta amsa musu lokacin da suke sanar da ita sun gyara ɗakin ,' saboda hayaniyar ƙawayen ta da ta cika ɗakin ,"    Nan suka kamo da baya tare da kama hanyar barin falon , kichiɓus suka yi da hafsa tare da wata ƙanwar baban su da ta titsiye ta tana mitar ta ƙira mata hamza ya zo ya ƙaro musu ma'aikata ,'domin aikin yayi yawa yafi ƙarfin ƴan aiki huɗu baza su iya bada abunda suke so ba ,"     Wayar ta sa taƙi shiga ga alama a kashe take watakila yana kan aiki ne ,"     Auntie hajja wayar ta sa bata shiga , amma ga waɗannan su biyun su ma ƴan gudun hijira ne kawai aje da su wajen da ake aikin su kama , kafin a ƙaro wasun ,"  ta furta hakan tana mai nuna mata su yakaka da suke ƙarasowa wurin ,'      Kallon su tayi sama-da-ƙasa , kafin ta ce    Toh su zo mu je ," Ku bita zaku je wurin aiki , ta furta musu hakan tana mai shigewa cikin falon ba tare da ta ko sake waiwayo su ba ,'     Jikin su ba ƙwari suka bi bayan wacce aka ce su bitan , har zuwa wani faffaɗan fili da yake ta chan baya ƙarshen gidan , inda aka kafa babbar rumfa aka kakkafa manyan murhu da takwane , gefe guda ga manya-manyan kasko da aka cika shi fal da mai ana suyar dubulan da alkaki , ga kuma manyan daruna an cika su fal da ruwan narkakken sugar ," aiki dai kacha-kacha ta ko'ina , da kallo yakaka ta bi hamshaƙan matan su kusan rai shida da suke tsaitsaye akan aikin , daga wuya zuwa kunne da hannuwan su sai ƙyallin gwalagwalai suke , yayin da daga sun buɗe baki hasken haƙoran gwal da suka yi ado da su a hakoran su yake ɗauke ido ," ko alama hannun su bai taɓa aikin ba , illa wasu jikkatattun manya mata su huɗu da suke yin duk wasu aiyukan wajen suna ta faman kai kawo ,"       Ga wasu masu aikin biyu ƴan mata an ƙaro su ,"    Cewar wacce suka biyo ɗin ,'    Waɗannan ai yara ne wane aikin kirki zasu yi da ya wuce wanke wanke da aike ? Inji ɗaya daga cikin matan ,"       Ko shi ɗin ma dai su yi , ai kuma zasu iya irin su soya abubuwa ma , "    Ke babbar ki zauna anan ki cigaba da suyar dubulan ɗin nan , ƙaramar kuma ga wanke wanken abubuwan da aka yi ƙwabin fulawar a ciki ki wanke ki kawo mana zamu sake yin amfani da su , cewar ɗays daga cikin ƴan aikin ,'   Cikin ƙasƙantar da kai suka haɗa baki wurin amsawa da toh ,' aiki ba sabon abu bane a wurin su , kuma basu jin tsoron aiki kome yawan sa ,"   Yakaka ta kama hannun falmata ta kaita wurin da aka tara wanke wanken manyan darunan silver da farantan silver manya da a zahiri sun fi ƙarfin hannun falmata ,      Ga bakin fanfo falmata ta sanya mata bakin tiyo ɗin da yake zubar ruwa akan hannun ta , kuma ga omo ga soso , ki wanke da kyau kin ji ?idan kin gama ki min magana kar ki taso ke ɗaya kin ga gurin akwai murhu ,!     Toh yakaka Daga haka ta je ta kama aikin da ita ma aka sa ta ,    Yakaka ta kama wannan aikin ta gama ta hau wancen , falmata tayi wanke wanke ta ƙara , har yamma suna wannan wurin , nan suka ci abincin rana da yin sallolin , gajiya tilis sun yi ta musamman ma yakaka da bayan ta ya riƙe ƙam , 'kawai karfin hali take amma a zahiri aikin yayi mata yawa , ' daga inda suke suna jiyo yadda ƙidan wakokin larabawa suke tashi ta cikin gida tare da tsinkayo hayaniyar jama'ah ,"   Karfe biyar aka sake kawo wani aikin wanda girki ne za'ayi na abincin dare a ainahin babban kitchen ɗin gidan , nan aka bar su yakaka suyi zaman gadi a wurin tare da ƙarasa tsoma sauran dubbulun da alkakin a ruwan sugar kafin a zo a juye su a ma'adanai a killace su, Har karfe takwas na dare suna wajen ,  zuwa lokacin hayaniya ta ɗan ragu a gidan ,saboda ɗaukewar kiɗa , sai dai shewa da dararrakin jama'a , falmata har ta fara gyanyaɗi saboda tsabar gajiya ,"babu abun da take so irin ta ji ta kwance bisa ƴar katifar ta amma ta san yau kam babu damar hawa wannan katifar , Chan sai ga hamshaƙan matan nan sun zo tare da wasu mata da alama su ma ma'aikata ne , nan suka ce su juye kome a manyan robobin tara ruwa , bayan sun sallami su yakaka babu ko sannu bare nagode , ! To meye ƴan aiki ne fa ? !   A gajiye liƙis suke cire takun kafafun su , duk sun yi laushi ,' ko magana sun gaza yi da juna burin kowaccen su ta samu muhallin ajiye haƙarƙarin ta     Tun daga bullowar su farfajiyar gidan hasken da yake wadace gal a wurin ya haske fuskokin su , babbar mashigar kofar gidan a buɗe take motoci sai kai kawo suke , Sun kawo tsakiyar farfajiyar kusa da ƴar hanyar da zata sada su da cikin sashin kwanan su , ya sanyo kan motar sa cikin gidan ,' idanun sa suka sauka a kan su , me suke yi a nan da daren nan wajen karfe tara ? Da sauri ya ajiye motar sa a mazaunin ta ya fito dags cikin motar yana bin su da kallo nan ya hango yadda suke duk a hargitse , kasan zanin falmata duk a jiƙe ,"    Ya taka da niyyar bin su , sai wasu ƴan uwan su mata su kusan rai biyar suka kutso kai cikin gidan , suna hango shi kuwa suka nufo shi suna gaishe shi tare da tsokanar shi kasantuwar su abokan wasa , nan dai dole suka tsayar da shi da ƴar hirar su ta zumunci ,   Zuwa lokacin da suka wuce su yakaka sun riga sun shige sun ɓacewa ganin sa ,    Shiru yayi a tsaye yana sake tunano yanayin da ya gan su ciki , " ba dai aiki aka sanya su ba ? Ya tambayi kan sa ,"      Nufar sashin sa yayi yana haɗa kamannin da ya gan su ciki da wanda yanzu ya ga yaran matan nan ƴan uwan sa a ciki , hakan ya tuno masa da abunda baki ɗaya ya manta "watau yiwa su yakaka ɗinkin fitar biki," al'amura sun haɗu sun chakuɗe masa , yanzu haka fita zai sake yi domin yana so ya ƙarasa shirye-shiryen kome kafin jibi da tawagar masu neman auren zasu iso daga garin abuja ," a ɗaura a basu matar su juya da ita bayan anyi walima ," sauran bukukuwan chan a abuja zasu ƙarasa bikin irin na su na soji ," Sannan a daren na yau yana so ƙwarai ya je yaga mahaifitar sa a unguwar da tayi bigire,' Duk yadda za'a yi dai goben zai samu ya saya musu kayan fitar bikin ko da ready made ne saboda lokacin yin ɗinki ya ƙure ,"  da wannan tunanin ya ƙarasa shigewa sashin sa ,' Su yakaka a cike suka tarad da falon duk kuwa da girman sa ,"yaran mata ne masu aure da marasa aure birjik a falon su da ƴaƴan su ,kowacce tana wace wance ," kaf ɗin su dangin juna ne , saboda ta bangaren mahaifin su manyan gida ne kuma shahararrun masu kuɗi kaf garin ansa kakan su wanda ya haifi baban su ,' Kamar jiran shigowar su hafsa take wacce take tsaye suna magana da wata ƙawar su ," tace    Yauwa yakaka dan Allah ɗauki Mopper nan ki goge duk illahirin cikin falon nan saboda akwai ruwa-ruwa kar a tattaka a faɗi ,"   Cikin juriya yakaka ta amsa    toh anti hafsa , Tas ta goge faffaɗan tiles ɗin ta ɗauraye mopper ta ajiye , ta dawo inda ta bar falmata a tsaye ,daga bakin kofa ,   Falmata zo muje ki gani na gano mana wurin kwana ," Wata ƴar siririyar hanya ta kai su da take bangaren hagu na falon da wata ƴar kofa ɗaya jal ta karfe , ta tsakanin karafunan kofar yakaka ta hango step ɗin bene , da yayi sama wanda a duk zaman ta a gidan kusan watanni biyu bata san cewa akwai bene ba ta cikin falon ," Kinga sai muyi kwanciyar mu anan tunda babu kowa , koh ? ******** Daidai da rana guda bai taɓa mantawa da ƙanƙanuwar yarinyar da ya lalatawa rayuwa ba , kullum sake ganin laifin kan sa yake a duk lokacin da yayi hasashen irin halin da ya bar ta da wanda a yanzu zata iya kasancewa a ciki ya kan shiga zullumin da yake kai ga hana shi walwala ,, Yayi nadama marar iyaka da ta sa har yau yana laluben neman sanin haƙiƙanin abunda ya same shi a wancen lokacin da har ya aikata abunda ko a mafarkin sa bai taɓa nuna masa shi youssouf zai aikata ba ,' idan akwai abunda yake bashi mamaki da sanya shi hamdala bai wuce wucewar wannan lamarin ko kuwa yace warkewar ciwon da ya kai shi ga aikata mummunan aikin ba , tun daga ranar da ya bar ta bai sake jin son kasancewa da wata mace a irin wannan yanayin ba , ya koma youssouf ɗin sa da ya san kan sa ," Ko ruwan burkutu yanzu ba sosai ya cika neman ta ba , sai jifa jifa jarabar sa da burkutun ya ragu da kusan kaso shidda cikin goma , kuma a lokuta da dama ko giyar company ma ya samu ya ɗan kurɓa yana jin kwaɗayin sa da barasar ya kau , Bulayin neman abunda zai sa shi ya goge laifin sa ko kuwa ya gyara barnan da yayi a wurin yarinyar , ya sanya shi ɗaukar tsawon lokaci bai sake waiwayar ta ba duk da cewa sau da dama a farkon rabuwar su ya sha ganin kiran ta ta layin da ya saya mata , kafin daga baya ya daina ganin kiran ,   Ya shiga damuwa da har ya sashi fara neman layin nata sai dai amsa guda yake samu kullum daga computer shine wayar tata a kashe take ," meya same ta ? Wane hali take ciki ? Wacce irin rayuwa take yi ?? Bai sani ba ! Zuwa lokacin da ya samar da abun da yake ganin zai taimaka mishi gurin gyaro ɓarnar da yayi , kuma sai yanayin aiki ya tsaida shi ,tare da sake yin nisa da inda take , amma ya ƙudurce ba zai bar kasar ba har sai ya gyaro barnar da yayi ta hanyar da shi yake ganin ya dace ," Dan haka da yanzu ya samu damar da zai iya fita daga wajen aikin ya taka zuwa cikin garin da take , domin a jiya da suka yi waya da tafeeda ya sanar da shi cewa ya shigo ƙasar nigeria a halin yanzu yana abuja , ' biyamuradin ya tabbatar masa da cewa zai halarci wurin ɗaurin auren , aina za'a yi bikin ɗaurin auren ? Amsar da ya bashi faɗuwa ce ta zo dai-dai da zama domin ya tabbatar masa da auran a jahar borno za'a ɗaura shi cikin birnin na maiduguri ," shikenan ma ba sai na zo har abuja ba , zan tsumaye ku cikin birnin maiduguri domun ai cikin garin nai bigire ," amsar da youssouf ya bawa tafeeda kenan ! Washegari , tun sassafe aka kaɗa kan su yakaka zuwa wurin aiki , ba'a ko bar su sun karya ba , sune shara wanke-wanke goge-goge basu nan basu chan , sai misalin sha ɗayan rana aikin ya dan tsahirta musu , suka shigo gidan suna rarrakaɓewa saboda kallon hadarin kaji da ake bin su da shi , Wanka suke so suyi su sauya kaya domin rabon su da wanka tun shekaran jiya , amma ko da suka shiga ɗakin da yake a zaman nasu , kawayen zainab da suke ta faman harƙƴallar su a ɗakin wasu na wanka wasu na karin kumallo koro su suka yi basu ko saurari zantukan da suke da nufin faɗi ba , haka suka fito jiki a sanyaye suka dawo bakin kofa suka rakaɓe ," Suna nan tsaye ya danno kan sa cikin sashin , yayi wankan sa fes cikin wani brown ɗin yadi mai shara-shara , sosai kayan suka ƙarbi kalar fatar jikin sa mai ɗan haske kaɗan , Akan su ya fara ɗora ido ," Me kuke anan fatima ? Ya na gan ku haka wani iri ? Anyi muku wani abu ne ? Kun kuwa ci abinci ? Ƙwallar da tuntuni take taruwa a idanun falmata suka tsiyayo ," lokacin da take saita idanun ta a sashin da ta ji tashin muryar sa Mun ci abinci yaya dakta , kuma ba'a mana kome ba , cikin ne babu wurin zama sosai shiyasa muke tsaye anan 'yakaka ta amsa masa , Wanne irin babu wurin zama ?ba ga ɗakin ku ba ku shiga ciki kuyi zaman ku mana ko kun fi son zaman parlour  ne?? Wannan Karon falmata ce tayi karaf ta amsa     Ai ƙawayen auntie zainab sun cika ɗakin , korar mu ma suka yi da muka shiga muna son muyi wanka mu chanja kayan mu ," ta furta hakan tana turo ɗan ƙaramin bakin ta bayan ta kumbura kumatu ,"irin su da ɗakin su ɗin nan," ( su falmata samun sarari tusar asuba )   Da kallon nazari yake bin su , yana ƙoƙarin boye ɓacin ran sa a gaban su kan abunda aka musu , To wai ya na gan ku kun yi datti haka ,? Ba dai aiki kika je kina ta faman yi ba a wannan yanayin da kike ciki ?    Tun jiya muke aiki yaya dakta yanzu ma muka gama na safe , cewar falmata , irin su a dole ga garkuwar su ,( ja'ira falmata an samu wuri ) Gabaɗaya bacin ran da yake ji ya bayyana saman fuskar sa , wanne irin aiki zasu sa ƴar mutane da ciki ? Har ya taka da nufin shiga gidan sai kuma ya jaa ya tsaya ,    Ina rahima ? Ya tambaye su ," Cikin rashin jin daɗin yadda falmata ta bayyana masa laifin ƴan uwan sa , yakaka ta amsa a sanyaye Tun jiya ban gan ta ba yaya ! Baice kome ba ya zaro wayar sa daga aljihu ya shiga neman layin rahima ," Bugu ɗaya ta ɗauka Hello big bro ina kwana ? Rahima kina ina kizo yanzu ina kofar sashin ku ,"    Toh ," ta amsa Ba'a cika mintuna huɗu ba sai ga ta ta fito daga cikin gidan ,"    Gani big bro ," ta furta hakan tana mai washewa yakaka haƙora gami da kashe ido ɗaya irin na shakiyanci ,"    Ki je da su ɗakin su suyi wanka su shirya ku zo tare ke da su ," ya bata umarni fuskar sa babu alamun wasa ,"     Toh ta amsa tana mamakin ɗakin nasu kuma zata raka su ? Kai big bro yana ji da baƙin nan nasa anya anya anya kuwa ,"  tunanin ta ya katse lokacin da ta ji yace ,"     Kice ga duk wanda ya nemi hana su yin abun da nace , umarnina ne a bar su suyi wanka su shirya ," nan ta fahimci akwai abunda ya faru ƙila hana su wanka aka yi , to wa ya hana su ?     Tana shiga ɗakin ta samu amsar tambayar ta domin suna sanyo kafa cikin ɗakin sofi wacce take rangaɗa kwalliya tace ,"      Kai kai ku koma , wai meye kuke mana sintiri kalen ku baɗa mana ƙwarƙwata ?? Daga kun zo wuri sai kun sauya kalan ƙanshin sa ,"cikin ran ta tana ji haka kawai ta tsani yaran ," ( karfin hali ) Da hannu biyu rahima ta dafe bakin ta kafin ta ce        lalala anty sofi baƙin big bro ne fa kuma ma daƙin su ne ," yanzu ma shi yace na rako su suyi wanka su chanja kayan su ,"        Baƙin ƴan gudun hijira ko dai bakin doctor ?    Wallahi baƙin sa ne shi ya kawo su ," Yakaka ku shiga kuyi wanka , ba kowa a bathroom ɗin ko ? Ta furta hakan tare da ɗan kwankwasa kofar banɗakin ,"   Falmata shiga ki fara yi ta furta hakan tana mai kaucewa mugun kallon da sofi take watsa musu ,"     Wata purple and black ɗin atamfa yakaka ta cirowa falmata daga cikin kayan su , sabuwa ce dal falmatan bata ko taɓa sawa ba , ta miƙa mata banɗakin lokacin da tace ta gama wanka , ita kuma ta fiddo wani pink colour ɗin yadi ɗinkin doguwar riga ta riƙe a hannun ta , Tsaf falmata ta fito cikin kayan da ɗinkin sun bala'in karɓar ta dinkin riga da siket ne na yayi wanda rahima ta zaɓar mata style ɗin ya zauna ɗas a kyakyawan jikin ta , baki ɗayan ƴan matan ɗakin suka bita da kallo lokacin da take wuce su tana nufar inda ta ji muryar rahima ta ƙira ta ," ",surar jikin fatima abar kallo ce   shine abun da rahima ta ambata aran ta lokacin da ta lura da kallon sake bakin da wayayyun ƴan matan suka bita da shi    Gyara mata ɗaurin ɗankwalin rahima tayi gami da rufa mata bakin mayafin akan kafaɗun ta wanda ta zame daga jikin ta  ," Cikin ran ta tana dariyar shirun da ɗakin ya ɗauka ," a hankali ta furta     Duk ta sumar da su ,! a gurguje yakaka ta yi wankan ta shirya ta fito , ta sanya ɗan madaidaicin hijabin ta fari mai hannu akan doguwar rigar da ɗankwalin ta fuskar ta fayau ko mai babu , Suka bar ɗakin ƙarƙashin rakiyar dogon tsakin da sofi ta bisu da shi ," a sarari rahima ta furta kya ji da shi ciwon ajali a ɗan yatsa , big bro dai kwalelen ki , ko dan wannan mugun halin naki ma zai sa ya tsane ki ,"aikin banza ,   Yana hango su ya nufi motar sa ya buɗe ya shiga ,"   Tare da rahima suka ƙaraso jikin motar ,"   Ta sunkuyo saitin sa ,   Big bro na cika aiki na , ? Baki cika ba rahima , ki shigo mu tafi ,    Ɗan jimm tayi , " bata son fitar domin tare da ƙawayen ta take suna shirye shiryen yadda anjima zasu tsantsare a wurin sisters day ,"    Shikenan je ki abin ki tunda baki son fitar ,"    Ta marairaice murya Big bro kayi hakuri ƙawayena zasu je nayi musu walakanci idan na tafi na bar su ,"    Toh rahima mai jama'a , agaida kawayen ,!       Ya furta haka yana tayar da motar sa bayan yakaka ta shiga gaba ta zauna rahima ta kamawa falmata ta shiga baya ,"    Kai tsaye ya nufi tata saloons da bashi da wani nisa sosai da gidan su ," Tun da suka tsaya gaban shagon bugun zuciyar yakaka ya sauya ," mikin da yake ciwo cikin ran ta ya dawo ɗanye , hotunan al'amuran da suka gudana a tsakanin su ya fara dawo mata , gata da soyayyar da ya gwada mata na ɗan lokaci suka bijiro mata son da take mishi ya yunƙuro da wani irin ƙarfin da ya sauya bugun zuciyar ta da har hakan ya jawo abun da ke cikin ta ya motsa da ƙarfi ," Har abada baza ta so wani namiji makancin son da take masa ba ita ta sani ta kuma haƙiƙance da hakan ," shi ɗin na daban ne cikin rayuwar ta kamar yadda son shi yake da wani irin ɗanɗano na daban a cikin ran ta ," wanda yake bata nishaɗi tare da kashe mata jiki a lokaci guda ," A hankali ta ɗaga kai tana kallon ƙaton board ɗin da yake kafe a gaba kaɗan da inda suka tsaya da motar su a gaban shagon ," karon farko da tayi ƙoƙarin haɗa baki ,"tunda aka fara koyar da su       A hankali leɓen bakin ta suka motsa                   TA-TA sunan wajen da yake ɗaya daga cikin wuraren da baza ta manta su ba a tarihin soyayyar su , wurin da ya sha gwada mata ƙaunar sa batare da jin nawin mutanen da suke kallon su ba , a gaban su ya nuna ita ɗin abar son shi ce abar ƙaunar sa wacce ya zaɓa ," kafin zuwa lokacin da kome ya sauya , kome kuma ya ƙare ya tsaya ƙem har zuwa lokacin da komen ya ruguje , rugujewar da ta samar da mummunan rauni a zuciya da gangar jikin ta , sai dai tana ji a jikin ta zuciyar ta kuma tana faɗa mata , komen bai ƙare ba kuma kome zai sabunta kan sa a watarana , sai dai abunda ta kasa samun tabbaci akan sa shine yau ne ko gobe ne komen zai dawo ?bata da tabbacin dawowar sa alhalin kuma shine komen da zuciyar ta ke ɓida a kowanne daƙiƙa bayan daƙiƙa . Wani irin farin ciki yaji lokacin da ya fahimci ta iya karanta sunan wurin da ya kawo su ," idan hakane tabbas kwakwalar ta mai saurin ɗaukar karatu ce , ƙwarai zasu shirya shi da ita , wata rana kuma zsi yi alfahari da ita , da alama ƴaƴan sa zasu samu haziƙar uwa ,"      Yes sunan wurin kenan    Tata saloons ," ya furta mata hakan da murmushi ɗaure kan laɓɓan sa , Da ido ta bishi tana mai jin haushin katse mata ɗan daddaɗan yanayin shauƙin da ta tsinci kan ta a ciki na tunanini abun son ta , Rufe motar suka yi bayan sun sun fiffito , yakaka ta kamo hannun falmata ta riƙe cikin nata , ," Bissmillah muje    Yace da su ," yana yin gaba ," Kamar yadda suka tsanmata gurin akwai mutane ,amma kasantuwar akwai wadatar ma'aikata nan take biyu daga cikin ma'aikatan suka taso taryar su , ɗaya daga cikin ma ta gane yakaka domin ta sha yi mata gyaran jiki ,"     Madam sannu da zuwa ta furta hakan tana mai yiwa yakaka murmushin sanayya ,     Ɗan yaƙe yakaka tayi a ranta tana furta ,'na shiga uku Allah ya sa kar su nuna sun sanni ,"    Madam kin kwana biyu baki zo ba , ma'aikaciyar ta furta haka daidai lokacin da take basu wurin zama ," Shiru yakaka tayi tana satar kallon doctor hamza wanda shi kuma hankalin sa ya tafi ga ɗayar ma'aikaciyar inda yake faɗa mata yana son ganin ainahin ita shugabar su ,"     Cikin girmamawa tace bari ta shiga ta sanar mata ," Ƴar wata ƙofar gilashi da take daga gefe a cikin shagon nan ma'aikaciyar ta shiga ,' bata ɗauki lokaci ba ta fito tace zai iya shiga wurin shugabar ta su ,"    A cikin mutunci suka gaisa da hajiya Ruma'yassa'u,  nan ya shaida mata kaya yake nema ready made na ƴan mata ,"     Ta tabbatar masa da suna da kaya masu kyau da inganci domin a jiya ma wasu ɗinkakkun kayan suka iso , dan haka sai wanda ya zaɓa tsakanin atamfa , leshi , shadda , yadi da sauran nau'ikan suturun mata , kawai abun buƙatar a zo da magnitude ɗin mai kayan ko kuwa shi kan sa , ya sanar da ita tare suke da waɗanda zasu sa kayan ," nan tace a shigo da su ,     Kallon sani take yiwa fuskar yakaka amma kasantuwar its ƴat kasuwa ce da take chuɗanya da mutane da dama ssi ta watsar da laluben inda ta san fuskar yarinyar , ta miƙe gami da cewa su biyo ta su da ma'aikaciya ɗaya dake tare da su ,"    Har ta ɗsn yi taku ta jiyo da murmushin nan nata mai haiba tana gyara mayafin kan ta tace ,"  akwai iyakacin adadin na kuɗin da keke so su ɗauka ne ?? Kuma shiga nawa zasu ɗauka ,"     Su ɗauki duk wanda suke so kuma kika ga ya dace da kowaccen su , " ki zaɓa musu ," shiga uku uku ,"    Toh shikenan ranka ya dade ," Ta cikin shagon suka ɓulla ta wata ƴar kofa zuwa wani kawatatcen shago mai zaman kan sa , ta ko'ina kayayyaki ne wasu a rarrataye wasu a cikin closets ɗin gilashi , kaya dai na kece raini tare da ɗaukar hankalin mai kallon su , Wurin zama ta basu akan wata doguwar kujera , bayan ta umarci ma'aikaciyar da ta gwada mata su mataki-mataki na jikin su , kai tsaye ta nufi faffaɗar closets ɗin ta shiga zaro wasu tsantsara tsantsaran lesuka masu ƙananun huji duk jikin su da mabanbantan kaloli da aka yiwa  ɗinkin wasu kyawawan dogayen riguna , buɗaɗɗu da tsukakku , gajerun hannu da dogaye , Tana daga inda take ta tambayi  size ɗin su nan ma'aikaciyar ta sanar da ita ,"  a take ta zaro huɗu daga cikin lesukan masu size ɗin da aka faɗa mata ,"         Bayan nazarin da tayi a matsayin ta na cikakkiyar malamar kwalliya wacce kuma ta san takan kwalliya da ado , ta zaɓarwa yakaka wata buɗaɗɗiyar doguwar riga mai rufaffen wuya turquoise color, ( ban San sunan launin a hausa ba  ) mai adon wasu siraran zare silver , Falmata kuma ta zaɓar mata ita ma wata doguwar riga da ta tsuke tum daga sama har zuwa cinyoyin ta ta ɓuɗe ta kasa , mai buɗaɗɗen wuya scarlet color, " da adon golden.  Kowaccen su dai-dai da tsawo da jikin ta , sannan ta zaɓar musu wasu atamfofi da aka yiwa ɗinkin riga da siraran siket sai dai ita yakaka tata rigar har kusan guiwar ta take yayin da ta falmata ta tsaya iyakar cinya ,  ta  yakaka background din ta dark red pattern din kuma aka yi da salmon and moss color , ta Falmata kuma background din fari ne pattern din kuma freesh grass and carnation color,  Sai yadika da suka ɗauka su duk biyu iri ɗaya see grean  da aka yiwa ɗinkin buba da single zane ,' Iyakar kyau kayan sun yi kyau , domin shi da kan sa doctor hamza ya yaba ya kuma ji daɗin gani zaɓin da hajiya ruma tayi musu , dan haka bai ji ƙyashi ba ko kadan ya lale makudan kuɗaɗen ya biya kuɗin kayan da ko a mafarki su yakaka basu taɓa hararo kan su a cikin irin su ba ," aka haɗa musu kayan har da gyalalluka bibbiyu da takalma masu kyau kafa biyu da ya sake saya musu aka sanya musu cikin babbar ledar mai ɗauke da tambarin TATA SALONS , Har zasu tafi ma'aikaciyar nan da ta gane yakaka tace   madam yau ba gyaran jiki ne da gyaran kai ??     Cikin tsanaki doctor hamza ya mayar da ganin sa kan yakaka wacce ta langwaɓe kai tana kifkifta ido duk wasu alamun rashin gaskiya sun bayyana a fuskar ta ,"   Bai hango kome ba bai kuma fahimci  komen ba illah hasashen sa ya bashi tabbacin tana so ayi mata gyaran jikin ita ma ,'bisa ga kallon da take masa mai kama da roƙo ," , Ayi musu gyaran jikin da wankin kai amma kar ayi musu kwalliyar nan ni ban cika son ta ba ,"  yace da wacce ta nace sai ta fasa ƙwan yakaka ,"     Toh yallabai ta amsa tana mai shiga rudu , da tayi zaton wani ɗan uwan mijin yakakar ne kamar yadda suka yi zaton biyamuradi mijin yakaka ne , sai dai kuma kalaman wannan na yanzu ya sata wasi wasi da chanki-chankin wanne ne mijin tsakanin farin dogon kyakyawan bamarɗen mai cike da ginshiri da ƙasaita irin na saraki , "  da kuma wannan matsakaicin mutumin wanda tarin nutsuwa da kamala gami da tsantsar ilmi suka bayyana kan su a tattare da shi ," ????? ( toh nima dai tambayar da nake yiwa masu karatu kenan ??? ) Gata dai ta gan ta har da ciki bayan tsawon watannin da suka yi rabo da ganin ta tabbas matar aure ce ,' Tattara gulmammakin ta tayi ta adana su gefe suka fara goge tare da sumulmule jiki , daga kafafu har kan su yakaka da falmata ," Basu suka bar wajen ba sai misalin karfe uku na yamma, iya wankuwa sun wanku fuskar su har sheƙi take , babu wata kwalliya da aka musu a fuskokin su sai fa siraran lallen da aka tsantsara musu yiryir a ƴan hannayen su da ƙafafu karkashin umarnin hajiya ruma a zuwan tukuicin da tayi musu na cinikin da aka mata tare da karrama abokan ciniki irin nata ," Kyau kam sun yi shi ƙamshi kuma sai tashi yake a sassan jikin su , falmata jin ta take kamar mai yawo a gajimare saboda yadda iska yake ratsa kowanne sako na jikin ta , yakaka kuwa lumshe ido tayi akan hanyar su ta komawa gida tana tuno wani yanayi irin wannan a tsakanin ta da biyamuradi , da hakan yake sanya ta sakin murmushi lokaci-zuwa-lokaci saboda hotunan fuskar sa da suke ta gilmawa ta idanun zuciyar ta Yayin da shi kuma doctor hamza yanayin da ya gan ta ciki ya sanya shi nishaɗi har shagala yake wurin satar kallon ta ya manta da tukin da yake yi ,'  sai fa idan motocin bayan sa sun matsa masa ham , Sun dawo sun tarar da gidan kamar yadda suka zata a cike danƙam motoci sai fita suke da ƴan matan da mata domin tayi party , Ganin cinkoson ya sanya doctor hamza sauke su daga bakin babbar kofar yace su shiga shi zai juya , su bar kayayyakin a cikin mota da daddare zai shigo musu da shi , su tabbatae sun samu wani wuri sun ɓuya daga idanun masu sanya su aiki , Duk da kusan kowa harkar gaban sa yake a farfajiyar wurin amma hakan bai hana falmata fahimtar yawan idanuwan jama'ah da yake yawo akan ta ba ta hanyar jin tsikar jikin ta na ta miƙewa , hakan ya sanya ta sake ƙanƙame hannun falmata Wacce itama ta sunkui da kan ta cikin  jin nawin idanun mutane da ta gani a kan su , Tun da suka ratso wurin take bin su da kallon mamaki , tabbas sune toh me kuma ya kawo su yaks gidan bikin zainab ?? Wai daman ashe da yaks ta gudu wani wurin daɗi ta samu ya sanya ta ji ta shiru da a farko ta dunga zaton wahala zai dawo da su da kafafun su ," bata buƙatar a sanar da ita tabbas yakaka da falmata suna cikin kin daɗi domin kuwa ta ga sauyi a tattare da su a zahiri ," shegiya yaks farar mace alkyabbar mata kyakkyawar mace kadara ,' babbar haja da ba'a raba ta da masu tayin saya ," ta furta a zahiri ," Kafin ta daddage ta kwalla mata kira daga inda take tsaye a jikin motar ƙawar su     Yaks Yaks Yaks , Chak suka tsaya daga ita har falmata kirjin su yana dakan sha tara ,"didif-didif-didifdif ,......! Toh fah , ga mafari yanzu ya fara , ga kuma azumin wata mai alfarma watan ninka ibadu ya ƙarato ,! Zan so na ƙara mana ko da page ɗaya ne kafin na rufe rubutun zuwa bayan ramadan insha Allah , menene ra'ayoyin ku ,?  Me kuma zaku ce ??  Nasan cikin shafin nan abubuwa da dama sun faru , a warware su mu tattauna , hakan tukuici ne agare ni , Wannan shafin nayi kyautar sa ga duk wasu ghost readers, masu tanɗe romon mafari ba tare da bada tukuici ba , ghost readers acigaba da gashi suya sai ranar da shafukan mafari suka Fara yi muku batan dabo 😂 Nagode muku baki daya!     [6/24, 10:59 AM] +234 701 013 7848: MAFARI ...... ( Hargitsin Rayuwa ) umm'muaz 25 BARKA DA SALLAH !ALLAH YA SA MUNA DAGA CIKIN WADANDA SUKA SAMU RABAUTA A WATAN RAMADAN ,"  ALLAH YA SA AYI BIKIN SALLAH LAFIYA , KUMA YA MAIMAITA MANA !   WANNAN SHAFIN GORON SALLAH NE GARE KU MASOYA ! Idan har kunnuwan su sun jiye musu daidai tabbas muryar samy baby suka ji ," wayyo sun shiga uku , meye ya kawo samy baby gidan ? Kada dai ta san doctor hamza ? Watakila ma ƴar uwar su ce , tunanin hakan ya sa yakaka jin jiri na kwasar ta ," Ya-yakaka ,"kamar muryar anti samy ta gidan madam ?" ," falmata ta furta hakan muryar ta na ƴar rawa tare da jin fargaba na rufto mata ," Muryar samy baby a kurkusa da su da suka ji wacce basu san lokacin da har ta ƙaraso ba ta katse amsar da yakaka ke shirin bayarwa ," Ni ce ba kamar murya ta ba , ta zarce da tambayar su ," Ashe kuna garin ? Yaks baki kyauta min ba , sai kawai ku haɗa kaya ku bar gidan babu bankwana ? Kika sa nayi ta bulayin neman ku har da farko na ɗaurawa madam saly laifi nace ita ta kore ku ashe ku kuka kori kan ku , sai daga baya na samu labari a bakin ƙawar ki wai daman kin ce mata zaku gudu kun gaji da aikin wahala ko ? Ina ku ka koma da zama yanzu ? Ina fatan inda kuka koma yanzun yafi inda kuka baro saukin rayuwa ? Ko da yake ma ai ga ku na gan ku shar da ku , meya kawo ku gidan nan ko biki kuka zo ? Muƙut ! Yakaka ta haɗiye wani busasshen yawun da yayi guntu a bakin ta , kafin ta tattaro ɗan guntun nutsuwar da ta rage mata ," Duk cikin dogon bayanin da samy baby tayi mata tambayar ƙarshe ta fi tada mata hankali ," aina suke kuma me suka zo yi gidan ??? ," Anan-anan kurkusa muke anty samy kuma ,unn unn Aiko mu aka yi nan gidan mu karbi saƙo , ta tsinkayi muryar falmata ta amsa tambayar ƙarshen ," da ya sa yakaka ta saki wata boyayyar ajiyar zuci . Sai dai me ? Muryar rahima ce ta ratsa wurin lokacin da take nufo su tana shirye tsaf cikin shirin zuwa party , Wow yakaka , fatima , kun gan ku kuwa ? Ɗanɗashi , haka kuka sha ƙunshi ? Ai da nasan har ƙunshi big bro zai kai ku ayi muku da na bi ku ," kai amma ƙunshin nan ya haɗu , wannan ai ko na amarya bai fi naku kyaun zane ba , ta ƙarashe zancen tana kashe wa yakaka idon ta ɗaya ,"da hakan yake tamkar al'adar ta ce ," Murmushin yaƙe yakaka tayi ,tana mai satar kallon samy baby wacce take bin su da kallo ɗaya bayan ɗaya da guntun murmushi akan fuskar ta ," Da murmushi rahima ta dubi samy baby ," Sannu anty samira kuma baku tafi ba har yanzu ? Bamu tafi ba rahima Samy baby ta amsa mata a takaice , Yakaka baza ku je party bane ? Na ɗauka big bro zai wuce da ku ta chan ,? A ah baza mu je ba rahima zamu shiga ciki mu taya su aiki sai kun dawo ," Yakaka ta bata amsa tana fatan ta wuce tayi tafiyar ta ," yau ɗaya ta ji surutun rahima ya fara gundurar ta ,' ! Ok sai mun dawo , Cikin sauri yakaka da falmata suka ɗaga kafafun su suna barin wurin tun kafin samy baby ta farga ," domun wata ƙawar su ta ƙaraso wurin ta janye hannun ta zuwa gefe suna ƙus-ƙus ɗin su ," Ta chan bayan ɗakunan gidan suka samu wuri suka zauna bisa takalman su a ƴar sassanyar inuwar yammaci ," Tab yakaka yau Allah ya rufa mana asiri kiris ya rage anti samy ta tona mana asiri , ai wallahi sam ban ji daɗin jin ta da nayi a gidan nan ba , ko me ya kawo ta kuma oho ? Ni har yanzu hankali na bai wani kwanta ba falmata , inaga kamar zata faɗa musu gaskiya akai na , watakila ma ƴan uwa ne ita da su rahima , " Allah dai ya rufa mana asiri yakaka , Ameen ! ta amsa tare da rashin kuzari Ba su suka fito daga maɓoyar su ba , sai da suka ga gari ya fara duhu , daga inda suke suna iya jiyo kiraye-kirayen sallar magariba , ga kuma hayaniyar da suke ji da ke nuni da cewa ƴan bikin ne suka dawo ,' daga wurin party ," Da rakaɓe-rakaɓe suka bullo ta cikin gidan , iya ganin su mutane ne ko ta ina da alama an samu ƙaruwar wasu baƙin ," Suna tsaye daga gefen kofar falon suna shawarar su shiga ko su koma maɓoyar ta su kawai su kwana a chan , tun da sun san dai ko sun shiga falon basu da takamaimai wurin kwana ," ! Yauwa , fatima , yakaka tun ɗazu nake neman ku , gaskiya kun wahalar da ni kusan ba ɗakin da ban duba ba a sashin mu , ina kuka shiga haka ?ko kun fita ne ? Cewar rahima wacce take ƙarasowa wurin su . Muna daga nan bayan ɗakuna rahima , kiyi hakuri bamu san kina neman mu ba ,! Har kun dawo ? Mun dawo , daman big bro ne ya ce duk inda kuke na neme ku , kun ci abinci ne ? Yakaka ta girgiza mata kai ," bamu ci ba ," Yauwaa toh ku zo muje ciki ga abincin ku chan na sa an ɗibar muku,! Ta cikin falon suka shiga suna biye da ita , suka nufi ƴar hanyar nan da ta hau sama ," suka bi ta ƙafar benen suka haura cikin wani babban falo wanda ya ƙawatu da kayan alatu , da manyan kujeru da tsadaddun labulaye , ga ƙofofi birjik a cikin sa ," Nan ɗin ma dai duk tawagar ƴan matan ne wanda ga alama sun yi ƙaura daga ƙasan ne sun dawo saman ," Dararrakin su da shewa sun cika wurin banda ɗan wani sassanya sauti da yake tashi a cikin falon ta cikin wasu mulmulallun sifika da suke a kowacce kusurwa na falon ," Daga bakin kofa su yakaka suka jaa tunga, rahima ta kutsa kan ta ciki ba tare da ta lura da sun dakata daga bin ta ba ," Kai tsaye ta nufi wata ƴar hanya sai ga ta ta bullo cikin ɗan Kitchenette ɗin duk da cewa babu wasu tarkace a ciki , amma Kitchen Cabinet ɗin kan sa abun kallo ne , kwarai Kitchenette ɗin yana da ɗaukar hankali , kamar yadda kome na sashin yake da mataukar tsari da kyau , fiye da na ko'ina a gidan , kai tsaye ta ɗauko ƴan madaidaitan coolers ɗin biyu ta fito da su ,' ", turis ta jaa ta tsaya lokacin da ta lura babu su yakaka a wurin ," Ina suke ??",    ta furta a sarari . Su waye ? Hafsa ta tambaye ta daidai lokacin da ta kai hannu tana ƙoƙarin karɓar cooler ɗin hannun ta ," Ta janye tana bata amsa da ," su yakaka da fatima tare da su fa muka hawo saman , wannan ma abincin su ne da big bro yace na ɗebo musu tun ɗazu ," Yamutsa fuska hafsa tayi ," Su waye kuma fatima ? Ita har ga Allah ta ma manta da sunayen su takamaimai ," C'mon bani abinci naci daman yunwa nake ji tun breakfast wani abun kirki bai sake shiga ciki na ba, " nima wallahi yunwar nake ji  cewar wata daga cikin ƙawayen su da take kishingiɗe a gefe ," Ƙanƙance idanu rahima tayi , Ki rufa min asiri malama kar ki jawo min fushin big bro , domin sai da ya daɗa jaddadamin na basu abinci... Kewaye su tayi ta wuce Bata saurari hafsa ɗin ba da take bin ta da tambayar Wai su waye ne waɗan da kike ta ambato ," Leƙawa tayi ta gan su a rakuɓe daga gefe ," Haa'ah ya kuka tsaya anan yakaka ? Ku shigo mana ga abincin naku ,! Toh ! Suka amsa suna masu sanyo kafafun su cikin falon ," A ɗage hafsa take jifan su da kallon tuhuma ,"kallon ku kuma me kuka zo yi nan ?? Ku zauna ,' rahima ta umarce su tana musu nuni da kan haɗaɗɗiyar shimfiɗar dardumar da take shimfiɗe tsakanin kujerun gurin ,'   A ɗarare suka zauna falmata ta matsu da jikin yakaka a saboda ji da take idanu sun yi yawa a wurin ,"    Yakaka ma kan ta a sunkuye yake saboda kallon banzan da sofi take jifan ta da shi a tun ƙarasowar su falon ,"   Ba tare da karsashi ba suke chakalar abincin duk kuwa da uwar yunwar da taje sasuƙar ƴan hanjin su da kuma yadda abincin yake da matuƙar daɗi ya wadatu da kayan girki na alfarma ," amma idanun jama'ah ya musu shamaƙi da jin dadin abincin ,     Ƙarar wayar rahima ita ta dawo da sofi duniyar tunanin da ta lula na son hasaso meye ne a tsakanin doctor hamza da waɗannan yakubayin talakawan ƴan gudun hijirar da har yayi musu matsauki a cikin gidan su ya kuma jiɓanci lamuran su da matukar muhimmanci haka ?? ," Hello big bro ,"   Gasu nan muna tare ma ," cin abinci suke ,"    Rahimar ta kai kallon ta ga yakaka wacce kan ta yake sunkuye ,"    Eh tana ci sosai ma ," to idan sun gama zamu zo yanzu ,"toh !        Yakaka wai inji yayan mu idan kun gama cin abincin muje yana ƙiran ku ,"    Toh suka haɗa baki wurin amsa mata ,"      Ba'a kai mintuna uku ba falmata ta zare hannun ta tare da faɗin ta ƙoshi , ita kuwa yakaka daman ba wani na kirki take ci ba ," dan haka ita ma ta miƙe bayan ta tattare ɗan abincin da falmata ta zubar ,"    Ƙarƙashin rakiyar kallon rainin da mafi akasarin ƴan matan wurin ke bin su da shi suka ƙarasa barin falon suna jin su wasai tamkar an cire musu wani mugun dafi da idanun jama'ar suka zuba musu ," daga yakaka har falmatan ba masu son mutane bane ," rahima ta jagorance su zuwa wurin da doctor hamza ya ce su same shi ," daga kusa da kofar sashin sa ,"     Tun kafin su ƙaraso ya nacewa kallon fuskar ta , da ita kuma ta shagaltu da kallon haɗaɗɗun motocin da suka cika harabar gidan wannan tana wace waccen a haɗuwa ,",   Suna ƙarasowa suka gaishe da shi , ya amsa tare da haɗa musu da tambayar babu dai wata matsala ko ? Kuma sun ci abinci sosai ko ?  Suka tabbatar masa da basu da matsalar kome sannan a ƙoshe suke ,"    Manyan ledojin da aka zubo musu kayayayyakin su da ya saya musu na fitar bikin ya miƙa wa rahima , gami da wata madaidaiciyar leda mai ɗauke da tambarin ', down town, "     Ungo rahima wannan kayan nasu ne na fitar biki , ki dunga taya su shiryawa ,    Ta sanya hannuwan ta biyu ta karɓa tana ƴar dariya ,"    Eyeeh gobe su fatima za'a chanchare  gaskiya fatima kin kwace min fada wurin big bro ," ta ƙarasa zancen da sigar zolaya , tana kashe idon ta ɗaya ,"       Ɗan murmushi su duk biyun suka yi cikin ran su suna jin daɗin kulawar da yake basu tare da kyautatawa , hakan ke ƙara sa yana sake girma da ƙima a idon su ,"      Ba tare da ya kula da zantukan ta ba yace ,"     Ga shi tare da miƙa mata ƴan mukullayen sashin sa , daga yau zuwa lokacin da za'a kammala bikin ku dunga kwana ke da su a sashi ne , daga ke sai su , bance ki haɗo min gayyar ƙawayen ki su ɓata min waje ba , ki kiyaye ,"      Ya ƙarasa zancen da sigar gargaɗi fuskar sa babu alamun wasa ,"    Toh    Kai kuma aina zaka dunga kwana ?   Tare da baƙi a sashin baba ya amsa mata yana barin wajen ," bayan ya basu umarnin su tafi su kwanta dare ya soma shiga ,"    Da zumuɗi rahima tayi gaba suka bi ta a baya ,    Tab lalle yakaka ku ƴan gatan big bro ne , baya fa son kowa ya shigar masa sashi , kana shiga zai fara korar ka kar ka kai masa datti , daga ka fita kuma sai yayi shara ya goge kujerun sa , bala'in tsafta ce da shi kamar mai aljanun tsafta ," ta furta hakan daidai lokacin da ta sanya mukulli ta buɗe ƴar babbar kofar mashigar sashin nasa ,"      Suna sanya kafafun su ciki ," kowaccen su tana gaskata kalaman rahima da ta ce yayan ta mai bala'in tsafta ne , saboda tuno haɗuwar su ta farko yadda ta kaya a tsakanin su , ta yadda ya fututtuke ya ci mutuncin su akan ƙazantar da falmata tayi masa a ofishin sa , wanda a lokacin da za'a faɗa musu doctor hamza mutumin kirki ne mai tausayi da kyautatawa irin yadda yake musu a yanzu zasu ce ,"ƙarya ne ," to ashe aljannu tsafta ne da shi , kamar yadda suka ji daga bakin ƙanwar sa ,"   Ƙamshin furanni tare da sanyin ban ruwa da aka yi a wurin zuwa wani ƙamshi na musamman da yake tashi a ƴar harabar sashin nasa suka haɗu suka bayar da wani irin yanayi mai daɗi tare da samar da nutsuwa ga zukata , "     Lumshe idanun ta yakaka tayi ta buɗe tana mai yawo da idanun ta a kowanne kusurwa ta wurin , ƙwarai yanayin wajen da tsarin sa suka burge ta ,"     Ƴar barandar da take ɗauke da ƙofar falon nasa rahima ta taka ta buɗe kofar tare da tura ta ta sanya kai tana cewa su yakaka ," su shigo ," Sanyi da kalolin ƙamshin da ɗakin yake suka sa falmata sakin wani gauron numfashi da tun shigowar su sashin take ta jaan iska ta hancin ta tana jin wata nutsuwa ta musamman na ratsa ta ," tsafta tayi a rayuwa ," Cikin shauƙin yakaka ta dunga bin falon da kallo ɗan madaidaicin falon da baya ɗauke da duk wani nau'in tarkace , kome ka gani a falon amfanin sa mai muhimmanci ne kuma yana bigiren da ya dace , Tun daga kan ƴan madaidaitan kujerun da suka kewaye falon tare da lallausan kafet har zuwa kan labulayen duk suna ɗauke da launi guda ne ,"ruwan madara ,"  sai gefe guda kuma girkakken gogaggen teburin katako ne shima ruwan madarar da ƴar kujerar sa wanda aka ajiye wata ƴar computer tare da tulin littatafai akan sa ," daga ɗaya sashin kuma ƙaramin firiji ne ,' daga haka babu kome a cikin falon sai sanyin AC da yake daga jikin bangon ɗakin sai kuma ƙamshin mai ɗakin da ya riga ya kama ko'ina na wajen ," A ƙasa suka zauna daga su har rahimar da take ta basu labarin party da suka halarta yau , " lokacin da take zazzage kayan da suke cikin leda ta ɗora da basu labarin , bikin da za'a yi na gobe har sai ya fi na yau haɗuwa da yin kyau domin a na goben har da tawagar ango da abokai/dangin sa waɗanda zasu iso a gobe da safe ,'    Woww wayyo Allah  yakaka wanɗannan ɗanɗasa ɗanɗasan rigunan dan Allah aina big bro ya sayo muku ,? Wayyo Allah ,"     Haƙoran ta a buɗe falmata ta fara bata labarin shagon da suka je ,' a ƙarshe ta zame ɗankwalin ta , baki siɗik ɗin gashin ta mai cika da tsawo tare da ƙauri ya bayyana ,"     Kin ga ma har kai sai da aka wanke mana ," ta ɗora da tambayar kin ga takalman da ya saya mana koh ? Su ma masu kyau amma ni dai kamar bazan iya sawa ba dana gwada Su naji  sun min tudu ,"    haba ! zaki iya sawa mana fatima , kuma wallahi ba ƙaramin kyau zaki yi ba ,     Wanne ne naki yakaka , wanne ne na fatima ,?    Ware mata su tayi Rahimar ta cigaba da santin kyaun kayan , a ƙarshe tayi alƙawarin taya su ƙwalliya tare da shiryawa ," inda har ta zaɓar musu waɗannan dogayen rigunan a matsayin kayan da zasu sa a gobe da yamma dai-dai lokacin da za'a fara gudanar da wushe-wushe a ɗora da sanya lalle ," ɗaya ledar ta jawo ta cire musu shawarman da take ciki naɗi uku kowacce ta ɗau ɗaya suƙa fara ci suna ƴar hirar su , har zuwa Lokacin da bacci ya ɗauke su ,"! ******** Misalin sha ɗaya na daren Alhamis biyamuradi youssouf ya samu shigowa cikin gari ƙarƙashin umarni da ya samu daga babbar headquarter su dake chan niemey inda aka bashi awanni arba'in da takwas akan ya je yayi uzurin da ya taso masa na gaugawa kamar yadda ya shida musu  ya dawo ,"   Shi ya tuƙo kan sa ya keto dazuzzukan da suke da matuƙar hatsari saboda ƴan tawayen boko haram da suka yi bigire a cikin sa ," À daren ya so yaje ya gan ta har ma su tattuna cikin awanni arba'in ɗin da yake da damar su yake sa ran zai iya fara gyara ɓarnar da ya tafka ,wanda idan ya samu haɗin kan yarinyar ya na san ran zai wanke hakkin ta da ya ɗauka  ya cigaba da istigfari ,  sai dai yadda garin ya ɗau shiru ya sanya shi barin tafiyar zuwa gobe da safe , ta yadda ko da bai same ta ba kai tsaye zai iya samun abokan hulɗar ta wanda su kuma kai tsaye zasu sada shi da ita ba tare da wata wahala ba , Da wannan tunanin ya samarwa da kan sa wurin kwana a hotel ɗin da ya saba zama a lokacin da yake sintirin a garin ,! ******* Tsabar jin daɗin bacci su yakaka ba su suka farka ba sai ƙarfe takwas da ƴan mintoci , hanzari yin sallah suka yi suna dariyar makarar su , duk yadda rahima ta so da suyi wanka a banɗakin dake cikin ɗakin nasa , ƙin shiga ɗakin suka yi , yakaka ta turje tace iyakar su falo nan inda suka kwana baza su shiga masa har uwarɗaki ba ,"cikin zuciyar ta tana gargaɗin kan ta akan su kiyaye zarmewa da yawa ," A gurguje rahima ta kintsa masa falon yakaka tana taya ta , suka kintsa falon tsaf tamkar yadda suka same shi ,rahima tayi musu umarnin da su bar kayayyakin nasu a ɗakin tun da nan ɗin yau ma zasu kwana ,!    Tana sanya mukulli tana rufe kofar falon nasa ƙiran sa ya shigo wayar ta ,"   Big bro ina kwana ,? lafiya rahima ,kun tashi ne ? Mun tashi big bro, " Gamu nan ma muna shirin fitowa ina rufe ƙofar falo ne ,"    Ki bar ƙofar a buɗe gani nan zuwa ku jira ni ," Toh tace tana sauƙe wayar daga kunnen ta ," A shiryen sa yake tsaf cikin ƙananun kayan da suka amshi matsakaicin jikin sa ," fuskar sa babu walwala sosai bayan ya amsa gaisuwar da suke mishi yace ,"    Ina zaku fita ku je da wuri haka ? Ku koma ku zauna a ciki har zuwa lokacin da za'a kammala abun breakfast sai rahima ta karbo muku ," Ba wani wuri zamu ba yaya dakta zamu shiga ciki ne , ko da aiki mu taya su ," ...   Ke da ba isasshiyar lafiya ce da ke ba shine zaki yi aiki ? Akwai masu aiki , ki kula da lafiyar ki ,' ku koma ciki ku zauna ban yadda ku fita daga nan ba ,' !    Big bro amma ni zan iya shiga ciki ko ? Saboda ka ga.... Sarkin surutu ke zaki iya tafiyar ki , amma ki bar musu mukullin a hannun su , idan anyi girki ki kawo musu , ban yadda ki ɗebo gayyar ƙawayen ki ba , ki kiyaye  . Toh big bro ta amsa tana jiran ta ji ya jerowa su yakaka sharuɗan kula masa da ɗakin sa , ga mamakin ta sai gani tayi ya juya yayi tafiyar sa ,      Da sassarfa ya isa ga motar sa ya buɗe ya shiga ya jaa yana mai barin harabar gidan ya nufi gidan da mahaifiyar sa tayi matsuguni cikin sa , zuciyar sa sam sam babu daɗi ,saboda saƙon da yake ɗauke  da shi akan harshen sa zuwa ga mahaifiyar ta sa ba mai daɗi bane    Ya rasa mai ya sauyawa mahaifin su ra'ayi bayan wahalar da ya sha kwana da kwanaki ,wurin roƙon sa akan ya amince mahaifiyar su ta tako gidan ayi bikin zainab ɗin tare da ita , da kyar ya samu nasarar shawo kan sa ya amince da ta zo tayi kwana biyu a kammala biki ta koma , sai dai a daren jiya ya sake birkice masa akan rashin amincewar zuwan ta gidan har ma yayi ikirarin idan har ya samu labarin ta zo zai mummunan saɓa mata ,    Fir yaƙi saurarar sa yaƙi yadda da duk wasu kalaman rarrashi da yake nufin yi masa ,'  yasan mahaifiyar su mai tarin laifuka ce , amma ƙwarai yadda mahaifin su yake nisanta su da ita yana matuƙar damun sa kome lalacewar uwa uwa ce ,"ba'a sauyawa tuwo suna ," Da wannan tunanin ya ƙaraso unguwar gami da karya kan motar sa ya gangara , kamar yadda yake a koyaushe unguwar cike take da yara ƙanana suna ta dawurwura a kan hanya , wasun su ko wondo babu , bare takalmi a kafafun su , batun wanka daman babu shi ," hakan ya sa yake tuƙa motar sannu a hankali yana sakin hon lokaci -lokaci saboda yaran da suke ƙaraƙaina , basa ko tsoron mota ,"    A ƙarƙashin ran sa kuwa har yau bai daina mamaki da son sanin dalilin da ya sa mahaifiyar su zaɓar rayuwar da take yi a wannan ƙazamtatciyar unguwar marar fasali ba , iyakar tunanin sa da tambayoyin da ya sha yi musu daga ita har abban su an rasa mai bashi amsa takamaimai , "   sai dai yasan koma menene ya faru ne bayan tafiyar sa makarantar gaba da primary ta gwamnatin tarayya ta kwana ,inda bayan dawowar sa hutun zango na farko na aji ɗaya , ya tarar da baki ɗayan rayuwar gidan nasu ta sauya , na farko dai bai tarar da auntie su RAHIMA a gidan ba sai sabuwar RAHIMA jaririyar ƙanwar sa ya tarar ,' abubuwa dayawa marasa daɗi ya tarar suna ta faruwa daki-daki wanda a ƙarshe ya jawo rabuwar auren iyayen nasu , da kawo karshen duk wata soyaƴyar da ya buɗi ido ya tarar iyayen su nayi wa junan su , hakan ya jefo mahaifiyar su cikin wannan rayuwar da take wanda yake jawo mata zagi da zargi tare da aibatawa daga dangin mahaifin su da shi kan sa ,," abun da hasashen sa yake bashi a koyaushe shine , koma menene ya jawo tarwatsewar rayuwar auren iyayen su yana da nasaba da auntie RAHIMA , wacce har zuwa yau da ake ɗiban shekaru wurin goma sha takwas babu wanda ya san ina take , a wane hali take cikin duniya ??? Wani ƙaƙƙarfan hon da wata mota dake biye da shi ta sakar masa shi yasa ba shiri ya kauce ya bashi hanya da mugun gudu motar ta wuce ,"hilux", ce baƙa mai ɗauke da baƙaƙen gilasan da ya sa ba'a iya hangen na cikin motar," Ɗan siririn tsaki hamza ya jaa yana aiyanawa a cikin ran sa wasu dai akwai su da wutar ciki ,    Parking yayi a gaban wani ɗan ƙaramin gida mai ƙaramar kofa dake ƙarshen layin ," ya kulle motar sa ya taka ya hau kan ɗan dandamalin  gaban gidan kafin ya leƙa da kan sa cikin ɗan siririn zauren ya rangaɗa sallama  har baki uku lokacin da yake kallon agogon hannun sa da yake nuna karfe tara dai-dai na safe  ," Karfe tara cif tayiwa biyamuradi youssouf a cikin rumfar madam saly , inda ya jaa ɗaya daga cikin kujerun wajen ya zauna ba tare da ya kula kowa ba ,  rarraba ido yake cikin nutsuwa yana neman fuskar ta a tsakanin fuskokin ƴan matan da suke ta kai kawo a gaban sa ," suna cigaba da gyaggyara tare da goge kujeru zuwa  kan teburan da suke cikin rumfar , domin ba'a riga an fara sayar da burkutu ba tukun , Karo na uku yagana ta ɗago kan ta tana sake kallon fuskar sa , tabbas shine wannan ɗan gayun balaraben mutumin da yakaka tace ɗan uwan ta ne ," Haɗa ido suka yi ta sakar masa murmushin da ke nuna alamun sanayya ,     Kallon ta yayi ya watsar gami da sake musƙutawa bayan ya daɗa ɗaure fuska tamau , cikin abun da bai fi mintuna biyar ba ya fara gundura da zaman , shi mutum ne wanda bai ƙaunar jira , yafi son daga ya buƙaci abu to ya samu ," Ajiye ɗan tsumman goge-gogen da yake hannun ta yagana tayi gami da nufo inda yake ," Sannu da zuwa malam. Yi yayi kamar bai ji ta ba yana nacewa kallon ɗaya daga cikin sabbin ƴan aikin da madam saly ta maye gurbin su yakaka da su ," farin ta ya jaa hankalin sa daga nesa yayi zaton ko wacce yake nema ce , sai da ta matso kusa ya fahimci ba ita bace domin wannan daga ganin ta ma hasken na bilicin ne ga fuskar tata wani wuri jaa wani wuri ruwan hoda wani gun kuwa brown ne ma , haka take dai dabbare-dabbare , ɗauke kan sa yayi dai-dai lokacin da ita kuma take farga da kallon da yake bin ta da shi nan take ta watsa masa signal da ido tana wani mokaɗe baki ! Gyara tsuyuwar ta yagana tayi ," Unm nace ka zo wurin yakaka ne ?? Maida hankalin sa yayi kan ta ji da yayi kamar ta ambaci sunan ta , sai dai matsalar shi bai wani riƙe sunan nata ba , amma tabbas kamar ya ji ta taɓa ambatar sunan ," Wata ɗiya nake nema , tana aiki anan doguwaa ce fara , tana da tsaga bisa ƙuncin ta , idan kin san ta ki sada ni da ita zan biya ki ," Karkaɗe jikin kayan ta yagana take lokacin da ta fahimci bayanin sa wanda yake sake tabbatar mata da zaton ta na ƙarya yakaka tayi mata da tace wai ɗan uwan su ne , domin ga shi ko sunan ta bai sani ba tabbas  wata alaƙa ce ta daban a tsakanin su ," YAKAKA TAYI CIKIN SHEGE MADAM SALY TA KORE TA DAGA GIDAN NAN, BABU WANDA YA SAN INDA TAKE . Ta furta hakan lokacin da take gyara zaman rigar ta cikin halin ko in kula , Wani irin abu biyamuradi ya ji tsuwww yana yawo a cikin kan sa tare da kalaman da yarinyar nan ta furta masa ," kusan bai ma fahimce ta sosai ba , dan haka ya saita idanun sa cikin nata tare da tattaro duk wata nutsuwa da yake da ita ya sake maimaita mata kalmomin da yayi amfani da su wurin tambayar ta ɗaya bayan ɗaya dalla-dallah kamar mai koya mata karatu ," Sake maimaita masa amsar tayi kamar farko ," lokacin da take taka kafafun ta tana barin wurin , tare da turniƙin kishin da ya tattare mata a ƙahon zuci , saboda tashin hankalin da ta gani a fuskar sa baro-baro yana nuni ne da kowacce irin alaƙa ce a tsakanin sa da yakaka mai girma ce ta kuma taka wani matsayi mai muhimmanci a wurin sa , " tare suka zo maiduguri da yakaka amma a sarari yake bayyanuwa yakaka ta fita sa'ar shigowa garin ,' tun akan wannan kyakkyawan ɗan gayun likitan da ya gigice a neman ta ta fahimci hakan ," wannan mai kama da larabawan kuma ko menene alaƙar sa da yakakar  oho ?? Ko ma menene ta sha alwashin sai ta rusa duk wani tubalin nasara a rayuwar yakaka ," Wani irin yanayi na ruɗani ya shiga da tunanin sa yake kufce masa da hakan har ya sa bai ma san lokacin da yagana ta bar gaban sa ba ," kalmar cikin shege kawai ita ke maimaituwa a ƙwaƙwalwar sa tana fasa kan ta tana sake dunƙulewa wuri guda tare da yin wajajjawa cikin tunanin sa ," wani irin ƙugi cikin sa yayi da yake bayyana halin tsoro da ya shiga lokacin da tunanin sa ya tattaru wuri ɗaya ya chanko masa yarinyar tana ɗauke da cikin sa ne ba cikin shege ba ," Kamar wanda aka tsikara ya miƙe tsaye akan kafafun sa yana wurga idanun sa kowanne lungu da saƙo yana neman yarinyar sai dai ko alamun ta bai gani ba kamar wacce ta ɓace , Wata irin damƙa ya kaiwa kafaɗun wannan koɗaɗɗiyar yarinyar da barin yagana wurin ya sanya ta tahowa gaban sa tana wata ƙwarƙwasa , Ƴar ƙara ta saki saboda yadda ƙasusuwan kafaɗar ta suka amsa da jin ruƙon soja ba da wasa ba ," muryar sa ta tsinkayo da wani irin yanayi da amon ta yake bayyana tsantsar tashin hankalin sa ," Ke wacece madam saly  ?  Yi maza ki sada ni da ita a yanzu yanzu ," A tsorace take kallon sa har sai da ta firgita ganin yadda fuskar sa tayi jaa jijiyoyin kan sa suka fito tar kore-kore ,    Ma-ma-madam bata tashi.... Tsawar sa ta katse ta ," Ki gwada min inda take nace yanzu yanzu ,"   T-toh sake ni muje na kai ka wurin ta ," Wucewa tayi gaba ya bita , har zuwa cikin gidan ƙofar ɗakin madam saly , ta tsaya daga bakin kofar ,"   Madam ina kwana ? Kin yi baƙo ne yake son ganin ki ," Daga ciki ta amsa , Wanne ɗan»»» yake nema na da sassafen kamar naci bashin uwar sa ban biya ba to bill..... Wata irin fincika ta ji anyi mata kafin ta fahimci meke shirin faruwa ta ji an watso ta waje daga ita sai wata ƴar guntuwar rigar baccin ta iyakar guiwa irin gumamar makkah ɗin nan , sillalliyar ƙeyar ta sai ɗaukar ido yake a hasken hantsi ," Kutuma..... Tace tana ɗago kan ta tare da miƙewa tsaye daga dunguren da tayi ,"     Arba tayi da biyamuradi youssouf , fuskar nan tasa yariman sa sak ," A take ta gane shi dan haka ta ƙanƙance ido ,' !    Lalle toh sannu uban uba na da zaka zo ka wani figoni haka toh idan ma ita karuwar taka ce ta aiko ka kazo ka mun wannan rashin mutuncin toh daga ita har kai kun yi kaɗan aikin ban...... Marin da ya waske ta da shi ya hana ta cigaba da bayani sai ma ganin duhu duhu da ta fara , ba shiri tayi faɗuwar ƴan bori tare da sanya wani kakkarfan ihu ," Ihun ta ya sa duk mutanen gidan rugowa da gudu zuwa wajen,  Har da ɗan liti da shima yake sawo kan sa cikin gidan ,  ya ɗebo da gudu har yana bangaje yagana wacce ita kuma take komawa baya saɗaf-saɗaf bayan da ta leƙa ta ga mutumin nan ne tare da madam saly," Meke shirin faruwa ,ko kuwa ya faru ?  da nake jiyo ihun giwar mata , ai wallahi ramar giwa kunyar daji , ace muna nan tare da ke kike sakin irin wannan ihun uwa wacce maciji ya sara ina macijin yake ??   Ya ƙarasa zancen yana bangazo larki ya faɗo tsakiyar filin Daidai lokacin da youssouf ya ɗago kafaɗun madam saly tare da saita ƴar ƙaramar bindigar da ya fiddo daga aljihun wandon sa a kanta ," muryar sa a kausashe a tsaƙanin maƙoshin sa yace mata Ina kin ka kaita ? Tana ina ? Duk inda take ki nemo ta , Wata irin zilliya ɗan liti yayi ya koma  bayan hema ya ɓuya, yana cewa      Na shiga uku an fasa aure nah ! Wata irin karkawar tsoro madam saly take ganin mutuwa kusa ," laɓɓan ta suna rawa tace Wallahi billahil azeem ka dai ji rantsuwar musulma kenan ko ? ba ni na kori yaks ba ita da kan dare ɗaya ta haɗa kayan su ita da ƙanwar ta suka bar gidan nan cikin dare babu wanda ya ga tafiyar su , ko jama'a ? ta maida tambayar ga mutanen da suke tsaye charko-charko an rasa mai cewa uffan a cikin su Sake danna mata bakin binɗigar yayi aka ,tamkar zai nitsar mata da shi cikin ƙoƙon kan ta yace ,"     Ƙarya kike ke kika kore ta kin san inda take , na baki awanni ishirin da huɗu ,zuwa gobe iwar haka ki tabbatar kin nemo ta idan ba haka ba kuwa sai na fasa ƙoƙon kan ki da harsashi , ya ƙarasa zancen da sakin ta ta faɗi ƙasa warwas ," Da sauri mutane suka dare suka buɗa masa hanya , a fusace ya wuce suka bishi da kallon tsoro ," Ihun madam saly ya dawo da hankulan su kan ta ,    Na shiga uku na lalace ni salaha ,wannan shigiyar yarinyar tsinanna ta zamar min annoba da masifa , ta bar gidan ma amma bala'in ta bai bar bibiya ta ba , wai ma wane ɗan .....uban ne ya faɗawa wannan mahaukacin farkan nata ni na kore ta??? Ta jefa tambayar saitin sa'a kerewa"sabuwar ƴar aikin ta da tayi masa jagora ,"    Da sauri ta ɗaga hannunwan ta biyu , ba ni bace sai dai ko yagana ce dan ita ce ta fara zuwa wajen sa suka yi magana ,"    Ina yaganar take ƴar .... Kira min ita , ai kuwa kafin cikar awanni ishirin da huɗun da ya ƙayyade dukkanin mu ba mu ga ta zama ba dole mu bazama neman ƴar** oh ni naga ta kaina , yaks ta sa raina cikin haɗari ! Billahi azeem yagana kin kusa barin gidan nan kema , " yau naga masifa da idanuna ,!      , liti aina ma kace kana ganin su kwanaki ?    Suna chan a jefe a Bakin kasuwa ! Matsowa yayi kusa da ita yana cewa     Mtss amma madam saly kin ban kunya , yanzu akan ƴar wannan barazanar da kurtun ɗan sandan nan yayi miki duk kika bi kika ruɗe haka ?? Yo kina da kamar mu ko soja ya isa tsorata ki ne bare wani ƙurtun ɗan sanda wanda daga kin manna masa ɗari biyu jal kin saye shi , kai ɗari ma ta ishe sa , ai wallahi ki bar ni da shi bari awanni ishirin ɗin su cika ya dawo kiga yadda zan miki maganin sa ah to meye ɗan sanda ne fa ?......      Madam saly wacce tun da ya tsugunna a gefen ta ya fara magana take hararar bakin sa , bata san lokacin da zuciya ta ɗibe ta cire hannu ta bige bakin nasa ba da bayan hannun ta ,"     Wani tsalle ɗan liti yayi Kutumelesi ,'saly fara," meye haka ?? Zaki kumburan baki ki munanan halitta ??  Ai ba ni na kar zomon ba da zaki min haushin kaza huce akan dami ," ya karasa zancen tare da rama harara da take masa ," Wannan abun da na maka ko karkaɗar ƙura bai kai ba akan wanda kurtun ɗan sandan zai maka muddin ka bari kuka haɗu ,"    Ta miƙe tana cewa ni bari na shirya mu bazama neman shegiyar ,"         Sai kun dawo ! Yace yana ƙoƙarin barin wajen ," domin shi dai babu shi a zuwa neman waɗannan tabaɗaɗɗun a cewar sa, ***** Duk yadda doctor hamza yake zaton mahaifiyar su zata ɗau lamarin hana ta zuwa wurin bikin zainab , abun ya wuce nan domin kuwa faɗa ta dunga yi ta inda take shiga ba ta nan take fita ba , wanda tun da yake da ita bai taɓa ganin tayi makamancin sa ba , duk kuwa da abubuwa dayawa da suka yi ta farauwa tsawon shekaru , a ƙarshe kuma ta rantse da Allah akan sai ta zo ita da mutanen ta na arziki wanda ta riga ta aika musu da goron gayya ta , idan ya so a kira hukuma su fidda su daga gidan ,! Ai ita ma tana da hakkin ta na uwa akan zainab ɗin . Ganin taƙi sauraran ban hakurin da yake yi mata hakan ya sa shi miƙewa cikin sanyin jiki , Amne ! ni zan koma , Allah ya huci zuciyar ki , Amin tace da shi tana kawar da kan ta gefe guda ,' tare da karkaɗa kyakkyawar kafar ta da ta ji ƙunshi zajir da shi har wani sheƙi yake yana ɗaukar ido akan farar fatar ƙafar ta , Langaɓe kai yayi ya tsaya yana kallon ta ,"   Banza tayi da shi domin tana jin ɓacin ran yadda a koyaushe yaran suke goyon bayan uban su akan ta tamkar ba ita ta haife su ba , Gajiya yayi da tsayuwa ya sake cewa    Na tafi amne.' Ka gaida mutanen gida tace tana miƙewa ta shige ɗaki Bayan ta ya bi da kallo kafin ya jaa ƙafafun sa a sanyaye ya fice , ko da ya zo jikin motar sa ma kasa shiga yayi ya tsaya yayi shiru ran sa baki ɗaya a jagule yake duk wani nishaɗi nasa ya kau ,       Fuuuuuw ya ji wucewar mota da matuƙar karfi , ya bi motar da kallo motar ɗazun ce dai , kaɗa kan sa yayi yana jimami lokacin da ya ga kiris ya rage motar ta buge wasu yara ,"    Allah ya kyauta ya furta a sarari yana shigewa cikin motar sa ,' ya jaa sannu a hankali ya bar unguwar ! ***** Tun safe Ƴan aiki da masu gyaran wurin da za'a yi taron wushe-wushe , suke kai kawo , yayin da masu dafa abinci ma basu zaune basu tsaye domin yin girkin taron baƙi , "tawagar gidan maza da shi kan sa ango da abokan sa da zasu iso a yau ɗin ,'girke-girke ake na alfarma , A gefe guda ƙawayen amarya ne zuwa ƴan uwan ta suke ta kai kawo tsakanin tata saloons da gidan domin yin kwalliya da gyaran jiki saboda kowacce so take ta burge so take ta jaa hankali , so kuma take ace ta fi kowa ," ! Amarya kuwa musamman aka ɗauko mai gyaran jiki da kwalliya daga tata saloons domin tayi mata nata shirin a gida ,' Duk kai kawon da ake yi fiye da rabin hankalin samy baby bai tare da ƙawayen na su , ya tafi ne ga tunanin son sanin haƙiƙanin ina su yakaka suke da zama , domin kuwa a yanayin su na jiya ta hango rashin gaskiya tare da tsoro ɓaro-ɓaro akan fuskokin su , Tayi niyyar ta titsiye su su faɗa mata gaskiyar ina suke da zama yanzu ? A hannun wa suke ? waye ya jiɓanci lamuran su tare da cikin jikin yakaka ? A ƙarshe ta ji dalilin da ya sa suka gudu sannan da manufar yakaka na barin cikin jikin ta wanda yayi girma sosai yanzu ya fito ,"! Sai dai ko alamar su bata gani ba tun da ta zo gidan ɗazu da safe , yau tazo ne da nufin kwana zuwa gobe da za'a ɗaura aure su juya tare da amaryar garin abuja inda a yanzu ta fi zama a chan saboda yadda harkoki suke gara mata sosai ta haɗu da manyan masu kuɗi suna sakar mata bakin aljihun su tana abunda ta ga dama , " Sofi ita ce ƙawar samy baby ta ƙud-da-ƙud , sosai ta su ta zo ɗaya , wasu halayya ta su suka dace da na juna , kuma ita ce ma ta gayyato ta bikin zainab ɗin a matsayin ta na babbar ƙawar zainab kuma sannan ƴar uwa ta kusa ga zainab ɗin ," Tunowa tayi da rahima wacce ta zo tayi musu magana lokacin suna tare , ta ji ta kama sunayen su , ta kuma musu maganar da yake nuna ta san su sosai , dan haka a bakin ta zata iya jin wani ɗan bayani akan su yakaka , ko da kuwa inda suke da zama ne , domin ita sosai take son jan yakaka cikin irin rayuwar da take a ganin ta gata take so tayi mata duba da cewar su yakakan basu da wani galihu , dan haka gara su tsaya da kafafun su . Ta maida duban ta ga sofi wacce tuntuni take zaune a gefen ta tana ta faman kiran doctor hamza yaƙi ɗaukar wayar , hankalin ta gaba ɗaya bai jikin ta domin tun da ta zo bai yadda sun tsaya sun yi maganar mintoci biyu ba , ' ko ta nace sun haɗu a hanya gaisuwar ta kawai yake ansawa ya wuce , a sarari yake gwada mata rashin kulawa tare da rashin ƙauna , amma ta gaza yin zuciya ta janye jikin ta saboda yadda zuciyar ta ta riga ta ginu da ƙaunar sa , duk wata harka da take da maza tana yi ne kawai dan jaraba ba wai dan kuɗi ko so ba , so ɗaya tak doctor hamza take yi wa , sai dai ta sani sarai shi kuma baya yi da ita , kuma ta sha alwashin dole shima ya so ta , ya kuma aure ta sannan duk wata macen da tsautsayi ya sa ta shigo rayuwar sa da sunan so zata iya kome domin ganin ta cisge ta daga rayuwar sa ko da kuwa idan ta kama ta ɓatar da mace ne ! friend ,     Ni ina rahima ne ? Ƙanwar ku ? Ki kira min ita idan kina da number ta zan tambaye ta akan wasu ," Samy baby ta ce ga sofi haka ,"    Sai dai ga alama sofi bata ji ta ba domin cigaba tayi da latsa wayar da ba kome take yi akai ba ,illa tana kallon tsawon lokutan da ta share tana ƙiran hamza yaƙi ɗauka , a ƙarshe ma da ta ƙira yanzu jin wayar tayi a kashe ," ji tayi wani irin ƙunci ya mamaye ran ta tana ji kamar an hura wuta daga ƙarƙashin zuciyar ta ," Taɓe baki samy baby tayi gefe guda tana jin haushin yadda ƙawar ta ta liƙewa wannan ɗan uwan nata likita , yana ta faman walakanta ta alhalin ga manyan masu kuɗi suna rubibin ta ,ta na jaa musu aji ,"    Mtss ta jaa tsaki gami da sanya hannu ta zare wayar da take riƙe a hannun sofi ,"   Haba mana friend  , ya kike bada kan ki irin haka ga ɗa namiji ? Kina bin sa yana walakanta ki , wallahi tun wuri kiyi wa kan ki faɗa , ni idan banda shan koko ɗaukar rai ban ga ma abun nacewa har haka agun wannan ustazun ba shi ba..... Wani irin kallo da ta ga sofi tana yi mata da idanun ta da suka kaɗa suka yi jaa ya sa ta kasa ƙarasa maganar da take nufin cewa ," Samira ki san irin maganar da zaki dunga faɗa min akan doctor , kin san wallahi zan iya ɓatawa da kowa akan sa dan haka ki kiyaye ,"   mtss samy baby tace tana ɗauke kai ," Dai dai lokacin da rahima ta hawo saman domin ɗaukar jakar kayan ta  ," Yauwa rahima zo mana ," Na'am anty samira ," Ni ina yaran na jiyan nan waɗanda na ga kun gaisa da su , su biyu yakaka da falmata aina suke ne ? Ƙira min su mana !        Anty samira nima ban san inda suke ba fa ,       Oh na ɗauka anan kusa suke , ? Ah ah .    Rahima ta amsa lokacin da take sunkutar jakar ta tana barin wajen ,   A sarari ta fara ƙunƙuni   Naƙi na ƙira muku su ɗin , ku sasu a gaba kuyi ta sasu aiki da aike kamar bayin ku ,ba kyau dai walakanta ɗan adam wallahi !      Ta cigaba da tafiya tana mita ," Sashin doctor hamza ta nufa wurin su yakaka , a kwance ta tadda yakakar ta miƙe , falmata na zaune daga gefen ta tana matsa mata kafafun ta da tace suna mata tsuku ,"saboda wahalar aiki da kai kawon da tayi kwanaki biyu da suka wuce ," Yau har sun ɗan yi kyaun gani daga jigatar aikin da suka sha ," tun safe basu fita a sashin ba rahima ita ta kawo musu abinci suka ci anan suka yi wanka , amma kayan jikin su suka maida domin rahimar tace musu su bari sai anjima idan an kusa fara wushe-wushe sai su yi kwalliya su je wurin .' Da dariyar ta ta ƙaraso ,    Yakaka , fatima ,  wai anty samira tana tambaya ta ku nace ban san inda kuke ba ," kun san ta ne ? Nagan ku tare jiya .     Anty samira ? Yakaka ta tambaya tana miƙewa zaune ,"    Ko dai anty samy ? Falmata ta sake tambayar ta , Ita , kun san ta ne ? Ai friends ɗin ta ke kiran ta samy baby , Tace wai kuna ina ,?  watakila aiki take son sanya ku ,"   Shiru suka yi aka rasa mai ƙwaƙƙwaran motsi ," samy baby tana son kawo musu matsala cikin zaman su a gidan nan ,!    Yakaka ta katse shirun , Mun san ta mun yi aiki a gidan da take kafin zuwan mu nan !   Oho toh ina ga shiyasa take neman ku ashe ta san ku ne ! ***** Karfe ɗaya cif jirgin da ya ɗebo tawagar angwaye ya sauka a maiduguri international airport , tun a Abuja tafeedah yake gwada kiran layin youssouf domin ya sanar da su tasowar su , da lokacin da zasu iso domin ƙwarai suka ƙagauta da su ga juna bayan tsawon watanni takwas da suka yi rabo da juna , sai dai wayar tana ƙara ba'a ɗauka ne , ji yayi hankalin sa na neman tashi domin ƙarshen wayar da suka yi a daren jiya misalin ƙarfe tara na dare youssouf ya sanar da shi ya kusa shiga birnin maiduguri , yana kan hanya . A maiduguri international hotel aka yiwa angwayen masauƙi yayin da iyayen kuma aka tafi da su wani babban gidan da ya kasance mallakin mahaifin su hamza ," Tun da youssouf ya baro gidan madam saly yake cikin halin gigita da ruɗani , dakyar ya dawo da kan sa hotel ɗin da ya kama ɗaki,  ganin abun yake kamar mafarki , duk shirin da yayi kafin zuwan sa ya rushe saboda wacce yayi domin ta bata nan ta ɓata ba'a ma san inda take ba tukun ," gefe guda sabon gingimemen al'amarin da yake neman kutso kan sa dole cikin rayuwar sa na barazanar zautar da shi ,"cikin jikin ta da babu wanda ya danganta shi da nasa ,illa zuciyar sa da tunanin sa da suke masa rubdugu wurin tabbatar masa da babu shakka cikin sa ne , saboda me ?? Yarinyar shi ya fara sanin ta ɗiya mace kuma har zuwa lokacin da ya bar ta bata tare da kowa sai shi ," Jayayya  yake da zuciya da tunanin sa akan lalle cikin ba nasa bane , ai ba jiya suka rabu ba , rabuwar su yanzu tsawon watanni shidda zuwa bakwai , zata iya yiwuwa bayan rabuwar su ta cigaba da bibiyar maza ne har ta ɗauki ciki , Sai dai sam zuciya da tunanin sa sun ƙi karɓar bangaren wannan hasashen nasa mai rauni ,"a kowacce daƙiƙa sake bijiro masa suke da dangantakar dake tsakanin sa da cikin jikin ta ," tsawon rayuwar sa bai taɓa shiga halin ruɗani irin haka ba , ya zama dole ya nemo yarinyar ko domin ya samu nutsuwar zuciya akan cikin jikin ta , nashi ne ko ba nashi bane  ?," Bai yadda ya danganta cikin da nasa ba , sai dai ya san ko da ba nasa bane samuwar cikin a tare da ita wani babban ƙalubale ne akan manufar sa game da ita da irin shirin da yayi na gyara rayuwar ta , shi bai san kome akan ta ba , amma yayi mata shiri mai kyau akan hasashen da yake kan dalilin da ya jefo ta rayuwa a wannan gidan da taje a matsayin ƴar aiki ," ko dai ta gudu a gidan su saboda rayuwar matsi da wahalarwa, ko kuwa auren dole , ko kuma tsantsar talauci da rashin galihu ya jawo mata neman kuɗi ra kowacce hanya ," Kowanne daga cikin dalilan nan yayi niyyar tunkarar matsalar ta ya magance mata ita , ya tsame ta daga rayuwar gidan saida burkutu zuwa kyakkyawar rayuwa , ya maida ta gidan su gaban iyayen ta ya gargaɗi iyayen ta akan sakaci da tarbiyyar ta idan ta kama ma yayi musu barazanar haɗa su da hukuma idan ya kama su da laifin wahalar da ita  ,  kuma ya tsaya mata tayi karatu, idan ta kama ya buɗe mata account ne ma zai buɗe mata wanda ko da ya bar nigeria saƙon sa zai dunga isowa gare ta , a ƙarshe ya bar mata numbobin wayar sa wanda a duk lokacin da wata matsala mai girma ta taso mata kowacce iri ce ta neme shi , Insha Allah zai magance mata idan ta kama ya tado da mutane ne ma daga chan ƙasar su zai turo , shi dai babban burin sa kar ya zamto a dalilin sa yarinyar ta faɗa mummunan rayuwar karuwanci wanda za'a dunga raba zunubin ta da shi , da ya fara lalata da ita ," Sai dai ashe ya makaro aikin gama kuma ya gama , ƙarshen lalacewa dai har ciki tayi ba tare da aure ba , " Sam yaƙi ya bawa kansa dama ya hasaso kan sa a matsayin uban cikin jikin ta , " ya san tabbatuwar hakan wani al'amari ne da zai iya yin ɗai-ɗaya da farinciki na duk wani mahaluki da yake da girma cikin rayuwar sa , a karan kansa kuwa tunanin sa yayi kaɗan wajen tsinkayo irin halin da zai iya kasancewa a ciki . Har tsuma yake lokacin da yake tunanin yadda zai sata a gaba ta kai shi har gurin ɗan iskan da ya ɗirka mata cikin , bai tunano irin azabar da zai gana masa ko da kuwa biyan ta yayi da amincewar ta yayi mata cikin ," a fili ya furta    Mtss doluwar watakila shima taimakon sa tayi ," tsabar kan sa ya ɗau chaji bai ma lura da wanda yake kiran sa ba ya ɗau wayar ya danna ta silent lokacin da ya ji tana neman damun sa da tsuwwa ," Ya ɗauki tsawon lokaci a ɗakin yana saƙa da warwara har bai san lokaci ya tafi dayawa ba sai da ya tsinkayi kiraye-kirayen sallah daga nesa , Wayar sa ya ɗauka dan ya ga lokaci anan ya tarar da miss calls ɗin tafeedah dayawa , ɗan dafe kan sa da ya fara sara masa yayi , shaf ya mance da lamarin bikin ma baki ɗaya ," bin bayan ƙiran nasa yayi mon amie kana lafiya kou ? Ina ka bar  téléphone ɗin ka ? je vous ai appelé mais vous n'avez pas répondu , Lafiya nake ɗan ouwa , kun kai ga isowa gari ? Muna a gari yanzou haka , Aina kun ka yi masauki ? Maiduguri international hotel,  , " kai kana ina ? Barwee hotel , nan tafeeda ya tambayi angon da yakasance haifaffen garin yanayin tsaro ya sa suka yi ƙaura daga garin zuwa birnin tarayya ,"  ko ya san barwee hotel ? ɗan ouwan sa da yake bashi labari chan yake da masauƙi , Nan take ya ce zai tura a ɗauko shi yanzu idan har ya shirya ,"   Da haka suka yi sallama bayan an sanar da youssouf tasowar driver , **** Karfe huɗu da rabi angwaye suka iso harabar gidan su amaryar inda anan aka riga aka fara wushe-wushe , dukkanin su sun yi anko na shuɗiyar shadda mai duhu ," kan su da jajayen hulunan dara ,"shigar su ta kanurai ! Ta ko'ina filin ya ƙawatu da adon gargajiya na kanurai , yayin da makiɗan ,"ganga kura" ( kiɗan kanurai na gargajiya )  suke tsaye daga gefe suna ta buga manyan gangunan su ga masu hura algaitun su na gargajiya suna hura ta tana bin kiɗan da mabanbanta sauti , Ƙamshin turaren wuta da aka sa a kowacce kusurwa na wajen yana tashi a hankali ta cikin electric burner ," Isowar angwayen bai ɗauki lokaci ba amaryar ma ta iso ƙarƙashin rakiyar ƙawayen ta waɗanda su ma suka yi ankon shuɗiyar shadda haɗe da baƙi ," ( danga-shaw ) sun rufe kan su da jaan gyalen ,"( mandil )," Amaryar kuwa wata farar haɗaɗɗiyar lafayyah ce ta naɗe jikin ta da shi ,  wuyan ta ya ƙawatu da babbar sarƙar mirjani haɗi da siririyar sarƙar gold ," Nan amarya da ango suka zauna a mazaunan da aka tanadar musu , yayin da ƙawayen amarya suka fara shiga filin rawa suna bin kiɗan malikii da yake tashi sannu a hankali suka fara rawa ta burgewa mai cike da ƙasaita , ɗaya bayan ɗaya abokan angon ma suka fara takawa zuwa cikin filin rawar kowannen su yana fuskantar  ɗaya daga cikin ƙawayen amaryar suna bin kiɗan tare da rawa kamar yadda tsarin rawar kiɗan malikii yake ,"   Nan take guɗa ta fara tashi daga bakunan manyan matan wajen , Jayayyar rahima taƙi ta ƙare da su yakaka waɗanda suka tirje kan su fa baza su fita wurin wushe-wushen ba , a ɗaki zasu yi zaman su ,"    Ai wallahi da na san haka zaku min ku ƙunshe cikin ɗaki da ban ɓata lokaci na nayi muku kwalliya ba , sannan shi da kan sa bro ai ya saya muku kayan ne dan ku sa kuyi kwalliya kuma ku shiga cikin jama'a ayi biki tare da ku ,    ta ƙarasa zancen muryar ta na bayyana jin haushin su , bayan kusan mintoci ishirin da ta kwashe tana bin su da lallama akan su zo su tafi ," A hankali yakaka ta miƙe tana sake gyara babban mayafin da ta lulluɓe kan ta da shi wanda shi da kan sa doctor hamza ya zaɓa mata shi , jikin ta sanye da doguwar rigar nan , kyau kam tayi sa iyakar kyau , tamkar irin wayayyun yaran matan nan da suka fara tashe a duniyar shahara ," cikin ta ya ɓoyu a cikin rigar  sai an lura da kyau za'a hango tudun sa,"     Yi hakuri Rahima , falmata ta shi muje ,"    Ni kam yakaka ko naje ma me zan yi a wurin ?  ni da ba gani nake ba...    Eh dai koma me zaki ce kizo mu tafi har ke ," ai zaki saurari kiɗan      Rahima ta katse ta da sauri Miƙewa ita ma tayi tana gyara ɗan siririn mayafin da ta rufe kan ta da shi , ɗan jim yakaka tayi ,"     Falmata ko dai na baki babban gyale na naga wannan kamar yayi ƙarami ? tana bin ƙawar ta ta da ido ganin yadda kayan suka mata cif-cif kamar wata babbar budurwa ,    Wai ma ji yakaka toh ai haka ake yayi bakya ganin rigar doguwa ce mai dogon hannu ? Dan Allah kar ki ɓata mata kwalliya ku zo mu tafi ,"     A hankali suke tafiya saboda takalman kafafun su da basu saba sa irin su ba , tafiyar kan ta a tsorace suke ji suke tamkar zasu faɗi ," Sun baro ƙofar sashin doctor hamza sun ɓullo ɗan wani siririn fili da zai sadar da mutum da harabar gidan falmata ta dogare ta ce ita daga nan zata tsaya , jin yadda take jiyo sautin kiɗan tamkar a gaban ta ," Rahima bata tsaya saurarar ta ba ta jaa hannun yakaka tana cewa     Ai sai kiyi ta tsayuwar idan kin ga dama ma ki koma ɗaki ," yakaka zo mu tafi ,     Ba da son ran yakaka ba ta bi bayan rahimar tana waiwayan falmata , wacce take murmushi jin yadda rahima take nuna jin haushin ta ," cikin ran ta tana ayyana taje gurin kiɗa tayi me ??  Ita ba gani ba bare tayi kallon jama'a ,' zata jira su anan har su dawo ,' Ta tsakankanin jama'a rahima ta dunga kutsawa riƙe da hannun yakaka har sai da suka bullo gaban filin ya zama , suna ganin duk wanda ke tsakiyar filin rawar ," Biyamuradi youssouf yayi tsaki yafi a ƙirga , ya kuma yi danasanin zuwan sa wurin wannan hayaniyar , tun asali daman shi ya tsani kiɗa domin ko nasu na masarautar su baya yadda su buga masa a gaban sa suna nufo shi yake sawa a tare su ya sallame su ," uwa uba tashin hankalin da zuciyar sa ke ciki , wanda duk wata ƴar sakewa da yayi suka ɗan taɓa hira da abokan tafeedan kawai ɗaurewa yake , sam bashi da nutsuwar zuci , tafeedan da kan sa ya fahimci hakan . Duk yadda yaso janye tafeeda su bar gidan ƙi yayi a cewar sa shi tsarin yanayin al'adar su ta burge shi dan haka zai ɗaukar wa mairamar sarki hotunan su haɗi da videos ya je ya nuna mata ,"    Da ace ya san kan garin ko kuma shi ya tuƙo kan sa ya zo , da tuni yayi tafiyar sa daga wajen , domin a halin yanzu ma chan gefe ya samu ya tsaya yana faman ciccin magani ,da ginshirin su irin na sarakai ,"  '"ah toh yarima anan wa zaka yiwa ?? Gani yayi gurin bai masa ba saboda yadda hankalin ƴan mata dayawa yake kan sa , dan haka kawai sai ya bi wata ƴar hanyar da ya gani daga gaba da inda yake tsaye kaɗan ," ba tare da ya san ina bane , sai dan gani da yayi akwai alamun rashin mutane ta wajen ,"   Ƴar siriyar hanyar ya shiga inda yake hango wani ɗan tudu da zai iya zama akai , sai da ya isa wajen ya lura da tsayuwar wata yarinya daga gefe a raɓe da jikin bango tana fuskantar ciki ,"   bai kula da wanzuwar ta ba ya zaro wayar sa ya shiga dubawa bayan ya zauna ,"   Tun takun sa na farko a wajen ta ji shi , ta cigaba da jin tahowar sa kafin daga baya ta ji an zauna a ɗan nesa da ita ,  jin shiru ya sa ta waiwayo ba domin tana son ganin wanene ba sai domin ta fargar da wanda ke wajen samuwar ta a wurin ,"   sun jima a haka shi ya manta ma da ya ga mutum a farkon zuwan sa wurin ,      Kamar ance ya ɗago kan sa , karaf ya sauke akan ta tana nan a inda ya gan ta tun farkon zuwan sa wajen ," idanun ta fes akan sa bata ko kifta su ,"    Shima kallon ta yayi sosai , ya ga dai ta tsare shi da manyan idanun ta da yake iya hango girman su da sheƙin da suke a sauran hasken ranar da take gaf da faɗuwa , " kamar shi take kallo kamar kuma ba shi ɗin take gani kai tsaye ba ," Yarinya ce a idanun sa bata wuce mairamar sa ba , a idanun sa ma sai ya ga tana yimar yanayi da mairamar yanayin yadda ta tsaya daga jikin bango alama fushi tayi taƙi fita zuwa wajen bikin nasu ,"        ɗan murmushi yayi tunowa da yayi da rigimar mairama yana jin kewar ta na taso masa ,"   Tsintar kan sa yayi da son yayi mata magana tun da ta rasa mai rarrashin ta ta huce,"    Ƙanwa ta ke baki gajiya ne da tsayuwa ??    Wara idanun ta tayi lokacin da ta ji tashin muryar sa , wannan ba doctor hamza bane ,toh WANENE ??? Da sauri yakaka take ratsa mutane tana son fitowa daga cinkoson gurin da ya sake ruɗawa da buɗa haɗi da sowa ana ɓarin kuɗi sakamakon shigowar ango da amarya cikin filin rawar ,"   dakyar ta samu fitowa ta nufi hanyar sashin doctor hamza , duk hankalin ta yayi kan falmata , bikin ya ɗauki hankalin ta har bata san ta ɗauki lokaci haka ba sai da ta ga duhun dare ya fara shigowa ta farga ! GAN,GAN ,GANNN ! GA ƁARAWO GA MAI KAYA , ƘAƘA TSARA ƘAƘA ??? DAFATAN ZAKU BAIBAYENI DA RUWAN RA'AYOYIN KU , GAME DA WANNAN SHAFIN , ME KUKA HANGO ME KUKA FAHIMTA ME KUMA KE SHIRIN FARUWA ?? KAI ABUBUWA DAYAWA FA , GA SUNAN DAKI-DAKI . BAN SAN KO KUN GANE BA ??? BARKA DA SALLAH ONCE AGAIN ! 😍🙏             [6/24, 10:59 AM] +234 701 013 7848: Mafari .... ( Hargitsin Rayuwa ) umm'muaz 26 Ji tayi an riƙo hannun ta ta baya , tana daf da ƙarasawa sashin doctor hamza , fuskar ta da murmushi ta juyo ga zaton ta rahima ce ,"     Rahima , Falmata nake son na duba , kin ga dare ya fara yi bana son .....    Sauran kalmomin ta maƙalewa suka yi a fatar bakin ta lokacin da tayi arba da fuskar samy baby a maimakon rahimar da take zato ,     An-anty samy  ke ce ??   Ba tare da samy baby ta saki hannun ta ba ta fara tafiya tana nufar cikin gidan da ita sashin su rahima , ba musu ta bita tana waiwayen hanyar sashin doctor hamza , da fatan ko zata hango falmata , yayin da ran ta yake cike taf da fargaban abun da samy baby zata bijiro mata da shi ," Waye ne a anan ? Falmata ta furta hakan tana mai sake wara ƙwayar idanun ta ," Shiru youssouf yayi  tare da kafe ta da ido ,   Watau dai ita mace kome ƙanƙantar ta mace ce ," ji wannan ƴar yarinyar ma wai dan kawai nayi mata magana shine har zata min gwalangwaso da fi'ili ta nuna ma bata ma ganni ba sam.,"  tsaki ya jaa gami da mayar da hankalin sa kan wayar sa , Sarai ta ji tsakin da yayi mata kasantuwar ta mai nisan ji , ko yaya abu yayi motsi tana iya ji tun daga ƙasan ran ta ," jikin ta taji yayi sanyi ," koma waye bai gane bata gani ba , " ba laifin ta bane ," Dan haka ta juya a hankali tana laluben jikin bango da nufin komawa ɗakin doctor hamza ," Kiran wayar sa da Tafeedah yayi shi ya sanya shi miƙewa bayan ya ɗaga kiran inda yake sanar da shi ya zo su tafi masallaci daga chan kuma su wuce masauƙin su sai kuma gobe su dawo ɗaurin aure ! Da sassarfa ya bar gurin da daman jin sa yake tamkar akan ƙaya ! Tsumu yakaka tayi a gaban samy baby wacce ta tsare ta da tarin tambayoyi wani kan wani ," Sake ɗagowa tayi a karo biyu ta dubi samy baby kafin ta muskuta cikin yin ƙasa da murya tace :    Antƴ samy a gidan nan muke da zama ni da falmata , kuma yaya dakta shi ya kawo mu ,"    Wanene yaya doctor ? Kina nufin likita yayan su zainab ? Gyaɗa kai tayi   Shi ne ! Daman ya san ku ne ? Ko ƴan uwan ku ne ??   Kawai ya taimake mu ne bamu san shi ba amma tun farkon zuwan mu garin nan tun muna sansanin mu yake taimaka mana !   Jimm samy baby tayi tana aunawa tare da juya zantukan Yakaka cikin ran ta ,"    Meye tsakanin ku da shi ? Ya taɓa cewa yana son ki ne ? Da sauri ta girgiza kan ta   A ah ni baya so na ! Bai tambaye ki akan cikin jikin ki ba ?  Me kika ce masa game da cikin ? Cewa yayi waye ya min cikin ? Ni kuma ban faɗa masa ba , tun daga ranar bai sake tambaya ta akan cikin ba , sai ya kawo mu gidan su nan , yace mu zauna , yana kula da mu sosai ni da falmata , har asibiti yake kai ni ayiwa baby photo dan Allah kar ki sa su kore mu anty samy bamu da wani wajen da zamu je a yanzu da ya fi nan ,    Ta ƙarasa zancen hawayen da take tarawa a ido suna silmiyowa ," Guntun murmushi tayi   Ni bazan sa su kore ku ba yaks , ki daina kuka ,!      iyeeh watau har hoto aka yiwa baby ? kice dai kin shirya zama uwa sosai yaks    jaan numfashi tayi kafin ta sake  wurgo mata wata tambayar da ta sa zuciyar yakaka tsalle ,"    Ya labarin yarima uban cikin jikin ki ko har kin haƙura da neman na shi kin daina son shi saboda kin samu gidan hutu ?   Ban - ban daina son shi ba anty samy kullum yana raina inason sake ganin sa , ban san yadda zan yi na gan shi ba ne ,! Ko kin samu labarin inda yake ? Murmushi tayi    Nasan inda yake yaks ! Zuruf ta miƙe tsaye batare da ta ji nawin cikin jikin ta ba ta matsa ta kamo hannun samy baby ta riƙe gam.,    Aina yake anty samy dan Allah ki kaini wajen sa , wallahi ina son shi , ina son na gan shi ki taimake ni ! Koma ki zauna yaks ba abun gaggawa bane , ki nutsu akwai maganar da nake so muyi da ke , amma....    Shigowar sofi ta katse abun da samy baby take nufin cewa ,    Da wani irin hargitsatsen kallo ta bi yakaka , kafin ta juya akalar hararar ta ta kan samy baby ,"    Ke kuma me ya haɗa ki da wannan koɗaɗɗiyar ƴar gudun hijrar ?? Ko wani aiki zata miki ? Nifa na tsane su yi sauri ki sallame ta duk ta cika mana  wuri da tsami da hamami ,"   Ba tare da samy baby ta amsa mata ba tace ga yakaka Ta shi ki tafi abin ki , Cikin sanyin jiki yakaka ta miƙe tana satar kallon sofi ,haushin ta na cinkushe mata rai ," sam ran ta bai so ba da zata bar gurin ba tare da taji wani ƙwaƙƙwaran bayani game da bature kam silum ba ,"  ta so ta ji ina yake da zama da babu abun da zai hana gobe ta je ta gan shi ko da kuwa da kwatance ne! Dai-dai tazo barin ɗakin ta waiwayo suka haɗa ido da sofi wacce take bin ta da kallon banza ," bata yi ƙasa a guiwa ba ita ma ta galla mata harara tana mai ƙarasa barin ɗakin ," Duka samy baby ta ɗakawa sofi a cinyar ta wacce take ta faman baloƙoƙo akan hararar da yakaka tayi mata sai faman zagin ta take tamkar zararriya    Ƙawata ke fa banza ce yanzu akan wannan ƙanƙanuwar yarinyar kike ta ɗaga murya haka ?  Alhali ma tayi tafiyar ta ," ko dai haushin kaza kike huce akan dami ," hala shi autan mazan ya miki abunda ya saba ?   Cisge ɗankwalin kan ta tayi jelar gashin dokin da tayi manyan kitson ghana suka watsu akan kafaɗun ta," Bari kawai kawata wannan ɗan tahalikin yana son ƙure gejin hakuri na akan sa , " bai san cewa akan sa kaɗai sashin zuciyata mai mutunci take iya tasiri ba , amma tunda yaƙi ta  mutunci toh fa ko da tsiya -tsiya wallahi sai ya so ni kuma ya aure ni , sannan na juya shi yadda na so a lokacin da na so , Naga shege ko shegiyar da ta isa yin min katanga da cikar burina , wallahi ko gyatumin sa sun yi tsororo !  Hamza nawa ne ni kaɗai , Da kallo samy baby ta bita tana nazarin kalaman ta tare da ɗauko kulawar da hamza yake bawa su yakaka tana haɗa su tare da yin dogon nazari , ita tasan wacece sofi tasan bala'i da kaidin sofi , bata fata ko kusa ko kaɗan ace wani sha'ani na adawa ya ratsa tsakanin ta da yakaka , wacece yakaka ? Bata tunanin ko uwar yakaka ta isa karawa da sofi akan abun da take ƙwalafacin so bare yakaka , tana tausayin yakaka da gaske baza ta so ba ta faɗo hannun sofi ta wannan mummunar hanya , ta sani sarai cikin ƙanƙanin lokaci sofi zata ɓatar da yakaka daga doron ƙasa ," Tunanin ta ya katse lokacin da ta ji sofi tana cewa    Wai kin kuwa san ma me yayi min ? Bata jira amsar samy baby ba ta ɗora ,    Tsawa fa ya min a bainin nasi , dan kawai na nemi ya tsaya muyi hoto ,"    Ta ƙuta , ai wallahi bashi ya ɗauka , zai kuma biya da tsada lokacin da ya shigo hannun na ,    Ta miƙe tana mai nufar bathroom , Da kallo samy baby ta bita ,"  ya zama dole tayi wani yunƙuri domin ganin ta hana wannan yaƙin faruwa tsakanin ƙaramar yarinya yakaka da sofi , dole ta zare yakaka daga rayuwar hamza muddin ta gano yana da manufar soyayya da yaks ɗin kamar yadda ta hasaso , " ai idan ka ga kare na sunsuna takalmi ɗauka zai yi ," kuma banza bata kai zomo kasuwa ," 10:30pm Duk yadda Tafeedah ya kai ga son sanin meke damun Youssouf da har ya firgita shi ya zama barazana ga nutsuwar sa , Youssouf ɗin yaƙi faɗi masa , iyaka yace masa ya gaji ne da zaman nigeria yana son komawa ƙasar su , wanda shi Tafeedah ko kusa zancen bai shige sa ba , tayaya Youssouf masoyi ga aikin sa kuma jajirtatcen jarumi a fagen daga zaƙwaƙuri wurin bawa ƙasar sa kariya tare da sadauƙarwa zai ce ya gajiya ? Babu shakka akwai wani abu wanda yayi girman da yake neman jirkita masa tunanin aboki da shi bai kai ga sanin wannan lamarin ba ," Kallon sa ya mayar ga Youssouf ɗin wanda yake kwance bisa gado ya takure cikin bargo gami da bashi baya , ji yayi duk wani ɗan kuzarin da yayi saura a jikin sa yana barin sa , bayan tsawon watanni tara da rabuwa da ganin junan su , yau sun haɗu amma babu wani armashi a haɗuwar ta su kamar yadda suka saba ya haka idan aiki ya shataa layi ya raba su , toh fa duk ranar da suka haɗu kusan raba dare suke suna hirarraki da dararrakin su ta hanya bawa juna labarukan bayan rabuwar su , " Youssouf amini ne a gare shi ƙari kuma ɗan ouwan sa ne na jini , amintakar su mai ƙarfi ce ta yadda idan ɗaya ya kasance cikin damuwa ɗayan ya kan gaza sukuni har sai sun haɗu sun samarwa da kan su mafita , damuwar sa a yanzu bai wuce yadda Youssouf ɗin yake kokarin boye masa abun da ke damun sa ba , da hakan yake baƙon lamari a tsakanin su  sai dai ko ma menene zai bi a sannu har ya kai ga sani , Ga Youssouf ɗin kuwa damuwa ce ta yi masa katutu , kan ɓacewar yakaka , mafi girman lamarin shine cikin da aka ce tana tare da shi , tunanin sa idan ba'a kai ga samun ta ba har ya bar nigeria yaya zai yi ?? Shikenan zai tafi ya cigaba da rayuwa alhalin wata na nan ta wanzu tana aikata babban zunubi ana raba musu tare ?? Wannan lamarin ya girmama a gare shi danasani kuwa yayi ta yafi sau shurin masaƙi , a bayan kowacce daƙiƙa damuwa ke sake masa lullubi , ya ƙagauta gari ya waye ya sake komawa gidan madam Saly ya ji yaya aka kwana  ?  Yawan damuwar ita ta bayyana kan ta ga Tafeeda wanda a zahiri bai shirya ba baya kuma fatan wani nasa makusanci ya san irin ta'asar da ya aikata a rayuwar sa , duk da yasan Tafeeda aminin sa ne , amma bashi da karfin guiwar sanar da shi wannan auka-aukar da yayi , to ma me zai ce ? Ta ina zai fara ? Ko babu kome shi ɗan nasaba ne , ɗan sarauta , ɗan manyan mutane wanda wurin su ake hangen kyaun tarbiyya tare da nagarta har mutane suyi koyi , yana jin zuciyar sa na nawi a duk lokacin da ya tuno da matsayin sa tare da martabar sa ga idanun tarin wasu mutane YARIMA ne shi wanda ake sa ran bayan shuɗewar wani lokaci idan da rai ya zama SARKI , JAGORA kuma SHUGABA abin KOYI , Anya-anya shi bai faɗa cikin wata babbar musifa ba kuwa ?? Ya ɗauki tsawon lokaci a haka yana kwance ba kuma bacci yake ba har zuwa lokacin da ya tabbatar bacci ya ɗauki Tafeeda , sannan ya miƙe gami da shiga banɗaki ya ɗauro Alwala ya zo ya fuskanci Al-Qibla yana mai fatan Allah ya kawo masa mafita ya kuma yafe masa zuban sa ! Kewar da take binne cikin ran yakaka tare da tsananin son biyamuradi youssouf sune suka yi toroƙo suka hana ta sukuni tun bayan rabuwar ta da samy baby , har ƙamshin sa ta dunga jiyowa lokacin da ta sanya kafafun ta cikin sashin doctor hamza wanda yayi mata jagora har zuwa cikin falo , illahirin tsukin wajen ya ɗauki kamshin kakkarfan turaren biyamuradi youssouf wanda yayi tasiri matuƙa wurin ƙarasa lugui-guita rarraunar zuciyar yakaka ta ƙarasa narkewa cikin so da begen biyamuradi , Hatta Falmata da Rahima sai da suka fahimci tana cikin damuwa , juyin duniya suka nemi sanin meke damunta ?? Tace musu babu kome a ƙarshe da ta ga sun damu ,musamman Falmata da ta gaza cin abinci dare na kirki , kamar yadda ita ma yakakar ta gaza ci , sai kawai tace kan ta ne ke ciwo , " nan ma dai wani sabon tashin hankali ne ga Falmata domin kuwa kalmar ,"sannu," bata yanke daga bakin ta ba har bacci ya ɗauke su ! Washegari  Misalin ƙarfe 8am Hamza ya ƙira Rahima a waya inda yake sanar da ita su buɗe masa ƙofa zai shigo ya shirya , "  daman sun riga sun jima da tashi dan haka.saƙon nasa kawai ta sanar ga su yakaka su dukkanin su suka miƙe , A bakin kofar sashin nasa suka haɗu da ladabi suka gaida shi ya amsa cikin gaggawa yana amsar ɗan mukullin sa da yake hannun rahima,'   Ku jira ni anan na gama shiryawa yanzu na fito , kar ku tafi ko'ina ,"  ya furta hakan yana shigewa ,"  har yayi ciki sai kuma ya kira Rahima suka shiga tare ,"      Hankalin yakaka ya kai ga manyan rumfunan da ta gan su a kakkafe a harabar gidan birjik wanda bata san lokacin da aka samar da su ba , ana ta faman shimfiɗa manyan dardumai da kilisai a ciki , babbar ƙofar gidan a wangale take ana iya hango kai kawon da ababen hawa suke akan titin da ya bi ta gaban gidan , wata mota ƙirar bus ce ta tsaya a ƙofar gidan , Manyan Mata ne su rai shidda suka fito daga motar sai kuma ƴan mata sun kai su biyar , dukkanin su suna yanayi da juna farare ne sol-sol dogaye , mafi akasarin su lafaya ce a jikin su wacce bata ƙarasa ƙasa ba iyakar sangalalen kafafuwan su, hannun su zuwa kafafun su da manyan zanen lalle , jazir " Manya-manyan jakar bacco sun kai guda biyar suka kinkimo zuwa cikin gidan , waccen da wannan sun kama wannan ma da waccen sun kama , uku daga cikin manyan matan ne basu sa hannu ba wurin ɗaukar kayan , Daga gefe suka tsaya tare da ajiye kayan hannun su , Ɗayar da ta tsaya biyan direban motar itace ƙarshen shigowa , Magana tayi musu kafin ta nufo sashin Hamza kai tsaye , su kuma suka dakata daga inda suke ,  duk abun da suke idanun yakaka yana kan su ta nacewa kallon su , yanayin su ya mata daban da na mutanen da ta saba gani , Idanun ta ya sauka akan matar da take nufo su , wacce ita ma hankalin ta ya kai kan su yakaka , sosai suke kallon juna ita da yakaka lokacin da take ƙarasowa gurin ," Da wata irin murya da ta fito da sauti sosai tace RAHIMA ,    Dai-dai da fitowar Rahima wacce jin sautin muryar da ko a mafarki baza ta mance ta ba tana ƙiran sunan ta ya sa ta ƙarasa takowa da gudun gaske ta rungume ta bakin ta na kiran ,   Amne ! Amnee !    Rungume Rahimar itama tayi idanun ta na nacewa kallon yakaka wacce ta sunkui da kai tare da riƙo hannun falmata , saboda wani irin yanayi da take hangowa a cikin idanun matar mai kama da idon wata wacce tayi wa farin sani ," A hankali ta zare Rahima wacce take ta murna tana dariya daga cikin jikin ta , Abnatay wacece wannan ?  Ta furta hakan tana nuna mata yakaka da hannun ta da ya sha awarwaro da jaan ƙunshi , Yakaka da Falmata ne , Su waye su ƴan uwan ku ne ? Da ɗan murmushi tace , " ƴan gudun hijira ne yayan mu ya kawo su ," ta ɗora da jawo hannun yakaka ,    Yakaka ga maman mu ," Nan take yakaka da falmata suka buɗe haƙoran su suna dariya kafin duk su kai guiwowin su ƙasa ,   Mama sannu da zuwa ina kwana , suka haɗa baki wajen gaishe ta ,"   Da sauri ta ɗago yakaka ,   Tashi - tashi yarinya ta babu kyau durƙuso a halin da kike ciki , sannun ku kuna lafiya ?    Lafiya lau duk su biyun suka amsa ," Ɗauke idanun ta tayi daga kan yakaka tana saita nutsuwar ta tace ga Rahima Ina yayan ku ?? Yana ciki ta bata ansa  Janye idanun ta tayi daga kan su falmata ,lokaci guda ta miƙa hanya zuwa ciki wajen Hamza ,  zuciyar ta na cigaba da kambama mata wasu kamanni masu karfi dake tsakanin yakaka da Rahimar ta , da a tashin farko da ta ɗaura idanu akan ta ta firgice , ƙewar  ƴar uwar ta na mamayar ta har idanun ta suna tara ƙwallar tunowa da ita a take taji gidan ya fara mata duhu , kome yana da sanadi kome yana da mafari , nan gidan , nan sashin shine mafarin kome , nan inda dugadugin ta ke takawa a yanzu shine mafarin tarwatsewar rayuwar Rahimar ta da yayi sanadin rabuwar su  , ko tana ina ?? Allah shi kaɗai ya sani .. sai dai jikin ta na bata Rahimar tana raye kuma zasu haɗu zata dawo gare ta , abu ɗaya ne fargaban sa ke guiguiyar ran ta kullum wayewar gari shine Rahimar zata dawo mata ne a matsayin Rahimar ta ƙanwar ta , ko kuwa zata dawo ne da ƙudirin ɗaukar FANSA  ,...... ? ****** Nan sashin Hamza , mahaifiyar sa tare da ƴan uwan ta da tsirarun ƙawayen ta , 'tayi bigire daga yau zuwa gobe da zasu yi tafiyar su ! tsakanin ta da dangin mahaifin su Hamza kallon nesa-nesa ne ko gaisuwar fatar baki bata haɗu su da kannen mahaifin su hamza ba ,tamkar ma gudun haɗuwa da junan su suke , saboda ta riga ta ƙullace su irin ƙullata mai tsanani domin tana musu ganin sune SANADIN KOME , kowanne daga cikin su su rai shidda yana da tabon sa a idanun ta idan aka cire UNCLE SALMAN wanda shi kuma a halin yanzu baya raye a duniyar ,... Su ma a ɓangaren dangin mahaifin nasu kowannen su ya ɗarsawa ran sa tsanar AMINA AL-ARABI SHUWA , saboda wasu manyan dalilai nasu ," Cikin awa ɗaya jal da haɗuwar ta da su yakaka , ƙaunar yaran ta gauraye zuciyar ta , dan haka bata jinkirta ba wurin tambayar su labarin su da na iyayen su , Cikin sakewar da suka yi da ita suka bata labarin su tirƴan-tiryan , kafin su gama tausayin su ya sa zuciyar ta tayi laushi , sau uku tana maimaita musu tambaya game da mahaifiyar su akan menene sunan ta ,    Amsar su ɗaya ce , su basu san ana kiran ta da wani suna ba bayan maman Yakaka , su kuma suna kiran ta Mama ,!      Ta jinjina da jin cewar mahaifiyar ta su kurma ce bata magana, ta kuma tausaya , sannan ta cire tsammanin da take ko yaran suna da wata alaƙa ta kurkusa da ita/da Rahimar ta , tasan Rahimar ta ba naƙasasshiya bace ba cikakkiyar lafiyayyar mutum ce , dan haka ta danganta kamannin da take gani na rahima tare da yakaka a matsayin kawai halittar ubangiji ," Karfe 10am aka ɗaura auren zainab da angon ta colonel Tahir Ma'aji , inda aka zarce da walima wanda mahaifin Amarya ya shirya ƙarƙashin jagoranci tare da kulawar Hamza , A daddafe Biyamuradi Youssouf ya tsaya aka ɗaura auren tare da shi , saboda hankalin sa da yake a tashe da son tafiya gidan madam saly dan jin ko an kai ga samun ta ,? "  A gurguje yayi wa ango gaisuwar taya murna , sannan ya jaa Tafeeda gefe , Ɗan ouwa ni zani koma bakin aiki ,ils ne me donnent que quarante huit heures , zuwa lokacin da nake issa bakin aiki , awanni sun kai ga cika ," Bai damu da kallon tuhumar da Tafeeda ke bin sa da shi ba , ya miƙa masa hannu suka yi musabaha , Idan ka cimma gidaa ka kiraye ni ɗan  ouwa ,' Allah shi kiyaye hanya ,saduwar Alheri Zame hannun sa daga cikin na Tafeeda yayi tare da juyawa ya fara taku domin barin wurin ," A takaice Tafeeda yace da shi ," me zan ce ga hajiya umma tare da mai martaba idan sun ka tambayeni halin da na riske ka ciki ??   Juyowa yayi da wani guntun murmushi a fuskar ka kace da su ,"    Yarima na a halin lafiya a bigire mai tsaro ,! Sannan ina miƙa gaisuwa ta a gare su tare da fatan Alheri ! Gyaɗa kai Tafeeda yayi yana mai juyawa ya shige taron jama'a cikin ran sa ya ƙudurce dawowa ya cimma youssouf su fuskanci matsalar sa tare , yanzu ma domin yana cikin ujila ne shi da kan sa awanni arba'in da takwas ɗin aka ba shi , dan haka su dukkanin su basu da isasshen lokaci a halin yanzu  ! Motar sa ya jaa da gudun gaske ya ɗauki gwadaben da zai sada shi da unguwar madam saly , Bai ko rufe motar ba ya taka ya shiga gidan , " a ƙufule ," sai dai tun daga bakin rumfar ya fara fahimtar sauyin da yake wurin domin dai babu kowa a cikin rumfar hatta kujerun cikin rumfar a tattare suke a gefe , da alamu yau ba'a shirin yin aiki ," Kai tsaye ya sa kan sa cikin gidan hanyar da ya bi jiya ita yau ya bi ya zo har bakin ƙofar ɗakin madam saly , har lau bai ga giftawa kowa ba tamkar gidan ba kowa ,"    Garam ! Ya ga ƙofar ɗakin madam saly garƙame da ƙwaɗo har biyu ƙarami da wani fankacece iri na rufe ƙofar babban gareji ,"   Duka ya kaiwa ƙofar ɗakin da ƙafar sa da matuƙar ƙarfi wanda ba domin ƙofar ta ƙarfe bace da ta karye,   Ya ɗaga murya yana cewa   Ina masu gidan ??   Ina masu gidan ?? Ko giftawar kadangare bai gani ba , bai buƙatar a sanar da shi , ya fahimci sun gudu ne ," nan take wani malolon bakin ciki ya maƙale masa a maƙoshi ," Murza fatar goshin sa yake yana kokarin saita kan sa lokacin da yake kan hanyar barin gidan cikin ran sa yana aiyana zai dawo kuma haɗuwar su ta gaba baza ta taɓa yiwa madam saly kai dama duk mutanen gidan kyau ba ,     Cikin takun da bai ko duba inda yake jefa kafafun sa ya bar gidan yana jin yadda zuciyar sa ke azalzalar sa da ya ɗan kora ruwa ko zai samu sa'ida azabar damuwa da yake ciki ta isa haka , amma tunowa da tafiyar ratsa daji da take gaban sa ya sa shi yakice tunanin shan barasa a wannan lokacin , ya fisgi motar da matsanancin haushin rashin cikar buri ya bar wajen bai ko kula da taron ƴan cha-chan da suke baje akan wata babbar tabarma daga ƙarƙashin bishiya a gefe suna faman yin karta tare da dara , da ya watsawa ruwan kwatami daga jikin su har zuwa fuskokin su ba ,     Wucewar sa kenan ɗan liti ya fito daga banɗaki inda yayi maɓoya , bayan ya tabbatarwa da su madam saly su watse kaf su bar shi shi kaɗai a gidan zai jira zuwan kurtun ɗan sandan , ayi wacce za'ayi ɓera ya zubda garin kyanwa! Banten uba ! Kuturi ai yau da na yadda ya ganni sai ɗan buzu na , ai wallahi da sai dai Baba malmo ya auro wata safara'un ta haifi wani ɗan litin ba dai ni ba ,! Chab kai ka ga mutum kamar safurarren doki ??? Yana tafiya haka - haka - haka ,"kamar jarumin sadauki a fagen daga ??    Ko a mafarki na gan ka ai nayi sadaka !      Ahayyeee saly fara ta zo ta lale min kuɗin gadin gida da nayi mata ta biya ni ,," kurtun ɗan sanda kuwa cewa zanyi na gama da shi ," ah to meye ?? Ko banza ai na shaƙi tsoro da bugun zuci, "  Rikicin duniya kuwa ai da me rai ake yin sa ehe ,! ****   Bayan kammala bikin zainab da sati guda doctor Hamza ya sanya yakaka a makarantar islamiyya da Rahima take zuwa , amma ta ta bangaren matan aure take zuwa kullum da safe karfe 8am.zuwa 12pm falmata kuma aka cigaba da koyar da ita arabi da bokon a gida ,' A makarantar yakaka ta san sabon sunan da doctor hamza ya laƙaba mata a matsayin sunan ta na yanka ,watau AMINA MUSTAPHA DILMARI , Sosai take mayar da hankalin ta kan karatun ta kamar yadda doctor hamza kullum yake gargaɗin su , a gefe guda kuma cikin ta na cigaba da bunƙasa ta yadda har girman sa ya so yin yawa dan haka a awun da ta je cikin satin nan aka hana ta shan su madara da sauran cimakar da take sa yaro ya girma sosai a cikin mamar sa ,"    Da wata safiya tayi shirin makaranta ta fito zata tafi sai ga motar samy baby ta tsaya a gaban ta , gaban kaɗan da gidan su doctor Hamza     Nan ta nemi ta shigo suyi wata maganar da take tafe da ita , tayi murna ma da suka haɗu anan waje ," ba musu yakaka ta shiga motar tana murna sake ganin samy baɓy a dai-dai wannan lokacin da ran ta yake cike taf da son sani game da youssouf    Nan cikin motar samy baby ta fara yiwa yakaka huɗubar da ta zamto kuskure na biyu da yakaka zata afkawa a rayuwar ta , A sanyaye ta fito daga motar bayan ƙarasowar su gaban makarantar , ta luluƙa a duniyar tunani , ta yadda har bata san lokacin da samy baby ta jaa motar ta tayi tafiyar ta ba ,"   Idan aka zo ga batun ƙaunar ta ga youssouf kome kunce mata yake , tana son shi sosai , yana birge ta fiye da kowanne mahalukin da ta taɓa cin karo da shi a rayuwar ta , amma anya ? Anya girman son da take masa ya kai mizanin da zata dai-daita shi da falmata ? Ƙanwar ta jinin ta ? Abar batun cikin jikin ta shi wani sabon abu ne da yanzu yake kan hanyar shigowar sa cikin rayuwar ta , duk da cewa akwai ƙauna irin ta ɗa da uwa a tsakanin ta da abinda yake cikin ta wanda tasirin son da take yiwa shi youssouf ɗin yake mamayar abun da yake cikin cikin nata tare da ninka mata ƙaunar son gudan jinin sa da ke tare da ita , To amma falmata ba ?? Falmata haske ce kuma sanyi ce sannan cikamakin farin ciki ce cikin rayuwar ta , tun asali akwai shaƙuwa da so mai tsanani a tsakanin su fiye da wanda aka saba sani tsakanin saƙo-da-saƙo na haihuwa , ya zarce ƙauna irin ta tsakanin ƴa da ƙanwa sai dai a kwatanta shi chakuɗuwar jini da soyayya irin ta tsakanin tagwaye wanda ƙarya ɗan adam ya zare wannan tsananin wannan son da shaƙuwar da ya samo asali tun daga ranar faruwar halitta a cikin mahaifiya , sai dai fa ikon rabbi ," Zata iya kome domin ganin ta samarwa da falmata farin ciki a kowanne bigire na rayuwa fatan ta a koyaushe ta hango farin ciki bisa fuskar miskiniyar ƙanwar ta , sai dai wannan lamarin da yau anty samy ta zo mata da shi , yarda da shi tare da yin aiki da shi tamkar ta ɗau takobi ne ta gille duk wani farin cikin da Falmata zata iya shinshinowa a rayuwar ta , tamkar ta kassara ruhi da gangar jikin falmata ne , wacece FALMATA idan babu YAKAKA ??? Ba ta san ta kawo karshen makarantar ba sai da ta ji ta kaiwa bango karo , Zamewa tayi ta zauna dirshan a cikin ƙasa gami da fashewa da kuka , a sarari take furta kalmar,"  bazan iya ba , bazan iya ba, ! **** Cikin satittikan da suka biyo baya samy baby ta cigaba da zirya tsakanin makarantar su yakaka inda take killace ta tana cigaba da cusa mata ra'ayin da take ganin zai iya tsallakar da yakaka daga faɗawa hannun sofi , ta hanyar yin amfani da kalaman yaudara da wayo ta cikin amfani da makahon son da yakaka take yiwa Youssouf , har ta kai ga nasarar samun haɗin kan yakakan ta wani ɓangare ba tare da ita yakakar ta san haƙiƙanin meke cikin ran samy baby ba, iyaka son youssouf tare da ƙwaɗayin son samun sa a matsayin miji ya sa ta fara amincewa da shawarar samy baby , ɓangaren zuciyar ta dake gargaɗin ta tare da tuno mata da so tare da tausayin dake tsakanin ta da falmata ya fara samun rauni , ! Soyayya tayi ƙarfi ta yadda ta fara rufe mata idanu ! Sannu sannu , yau da gobe zuciyar yakaka tare da taimakon huɗubar samy baby da ta shaiɗan , ta ƙeƙashe da son ganin cikar burin ta na mallakar youssouf a matsayin mijin ta , kamar yadda samy baby ta wanzu tana ƙara ƙwaɗaitar da ita , bata ko duban hidindumu tare da gatan da doctor hamza yake gwada masu ita da ƴar uwar ta musamman ma ita da komen ta yake mai matuƙar muhimmanci agare sa , ko sau ɗaya bai taɓa burge ta ba , Koyaushe ɗaukar sa take a matsayin me kirki me TAIMAKON SU, hankalin ta a kullum daɗa tafiya yake ga youssouf wanda a yanzu hoton sa ya zama abun ɗebe kewar ta kullum dare har ma ta kan ɗan zanta da hoton idan dare yayi nisa wutar so kuma ta ruru iya ruruwa , sai ta fara sakin sambatun so , Sai dai tana ƙoƙari wurin boyewa musamman ga doctor hamza , wanda watarana a cikin ranaku ya kamata tana kici-kicin ɗaura agogon da youssouf ɗin ya bar mata a tsintsiyar hannun ta , ta shagala cikin bege sai murmusawa take har haƙoran ta na bayyana , sakamakon yadda idan ta ɗaura agogon yake zamewa daga hannun ta idan ta sauke hannun ,  sai tayi maza ta taro agogon ta chafe shi ta sake mayarwa cikin hannun ta , tana lailaya shi kamar tana ganin fuskar youssouf ɗin a jiki , Ya ɗauki lokaci dogare a bakin kofar yana kallon ta cikin shauƙin ƙauna , sosai tayi kyau a idanun sa tana sanye da atamfa buɗaɗɗiyar riga da zane, tayi ƴar madaidaiciyar ƙiba ta buɗu kaɗan , sai ɗaukar ido take Hankalin sa ne ya koma kan agogon da take wasa da shi a hannun ta , yana iya hango girma tare da ƙƴallin agogon daga inda yake tsaye ," ya shaida agogon maza ne ,"  Takawa yayi ya ƙarasa cikin falon bata lura da zuwan sa ba , sai gani tayi hannun sa ya riga ɗayan hannun ta chafe agogon lokacin da yake silmiyowa daga tsintsiyar hannun ta ," Ɗaga agogon yayi yana ƙare masa kallo daga gani ba tambaya agogon mai matuƙar tsada ne , da samun irin sa sai a hannun goggagun attajirai ," Cikin taushin murya da nutsuwar da take mahaɗin cikar kamalar halittar sa yace ,"     Agogon waye ? Shiru tayi tare da sunkui da kai, tun usul ƙarya bata cikin halayyar su , basu ma san yadda ake yin ta ba idan ba yanzu da duniya take ƙoƙarin koya musu ba ,"   Ganin sa ya janye daga kan agogon ya maida kan ta , tare da ɗan ƙara sautin muryar sa ,    Wannan agogon na waye ne ?? A firgice ta ɗago kan ta jin kamar ya mata tsawa , matuƙa take shakkar sa tare da gwada yi masa biyayyah Ba-ba-baba Agogon - agogon Baba ne !   Ta harhaɗo kalaman da suka fito a baibai ,"  idanun ta na yin ƙwalƙwal . Agogon Baba ?   Hamza da Falmata suka haɗa baki wurin tambayar ta ! wacce take ƙarasowa wajen da lalube daga cikin ɗakin saboda jin tashin muryar doctor hamza domin ta gaishe shi , Agogon Baba ? Yakaka ina agogon Baban mu ? Daman Baa yana da agogo  ,       Falmata ta furta hakan cikin tsananin murna kasantuwar ta mai matuƙar ƙwalafacin iyayen ta , hakan ya sa ta ma manta da abun da ta fito yi ,"gaishe da doctor hamza ," ta himmantu wurin son a bata agogon ta riƙe , doctor hamza ne ya ɗaura mata agogon bisa hannun ta , bai sake cewa kome ba ya juya yana barin falon zuciyar sa cike da wasi-wasi akan kalaman da yakaka ta furta na dangana wannan tsadadden agogon ga mallakar mahaifin su , A sanyaye falmata ta ɗago kai daga barin shafa agogon da take yi ta saita idanun ta a inda take zaton yakaka na zaune ,     Yakaka kika ce wannan agogon Baa ??     Da ido yakaka ta kafe ta kamar tana son ta gyara mata sokuwar ƙaryar da tayi ," wanda ta hango rashin yarda da zancen nata ƙarara a idanun doctor hamza    Miƙa hannu tayi ta zare agogon daga hannun falmata ,    Falmata muje ɗaki na kwanta ki ɗan danna min kafafuna ciwo suke min ,   Da sauri ta amsa da   toh sannu yakaka Tun daga ranar yakaka take koƙari wurin boyewa kowa duk wani abinda ya shafi soyayyar da take yiwa youssouf ciki kuwa har da Falmata , Da samy baby kaɗai take hirar sambatun soyayyar youssouf , wacce take daɗa ƙaimi wurin shiryawa yakaka gadar zare , tare da bugun cikin ta a koyaushe tana jin tsakanin ta da doctor hamza , irin kulawar tare da hidimar da yake yiwa yakaka yake sake bata tabbacin zaton ta gaskiya ne , doctor hamza son yakaka yake , soyayyar kuma mai tsanani ta aure , wanda a koyaushe idan ta tuno sofi da irin mahaukacin son da take yi masa da irin mummunan alwashin da ta sha a kan sa , sai taji abinda take kokarin yi da nufin raba tsakanin sa da yakaka dai-dai ne, a ganin ta taimakon yakakar zata yi , har ma tana danganta yunƙurin ta a matsayin CETON RAI ,"  Lokacin da yakaka ta shiga watan haihuwar ta hamza ke sanar da ita daga wannan satin zata daina zuwa makaranta , baza ta dunga zuwa ko'ina ba daga awu , sai dai ta fita motsa jiki da dare , Da farko ta shiga damuwa , da hukuncin da ya yanke na hana ta zuwa makaranta ganin cewa a makarantar take samun damar haɗuwa da samy baby duk lokacin da samy baby ta so ," Amma lokacin da ta sanar da samy baby sai ta ga bata wani damu ba , suka cigaba da hirar su da fiye da rabin hirar maimaici ne tare da tisawa akan yadda tsarin samy baby yake da yadda kome zai kasance , har zuwa gamuwar ta da muradin zuciyar ta kamar koyaushe yakaka ke ƙarasa hirar da sambatun yadda haɗuwar tasu zata kasance da youssouf da ɗokin zuwan ranar , Bayan gama hirar su , sai samy baby ta ciro ƙaramar wayar ta , ta kamo hannun yakaka ta danƙa mata ,"     Zamu cigaba da tattaunawa akan waya yaks , saboda kin ga bana son mutanen gidan su san da alaƙar mu domin kar a zarge ni har a bibiye ni bayan kammaluwar kome , ki tabbatar babu kowa a wurin a duk lokacin da zamu yi waya , ki dunga min flashing idan kina son magana da ni , sannan kuma daga mun gama magana ki dunga kashe wayar , kar ki bari kowa ya san da wayar , Idan chaji ya kusa ƙarewa ki sanar da ni , ni zan san hanyar da zan yi na karɓi wayar nayi mata chaji ," Abu na ƙarshe shine kar ki manta da tsarin mu ko cikin dare kika ji ciwon haihuwa na zama mutum na farko da zaki fara sanarwa kafin kowa , kin san dai shirin mu zai fara ne daga haihuwar ki ,  ai kin gane ko ?   Naji anty samy kuma bazan manta duk tsarin da kika shirya min ba , nagode sosai da taimakon da kike min a kullum tunda muka haɗu , Allah ya saka miki da Alheri ,! Murmushi mai wuyar fassara samy baby tayi,     Ameen yaks , Tun bayan da doctor hamza ya sawa yakaka dokar hana fita unguwa , ya zama kullum da dare tare suke fita ita da Rahima , da misalin karfe 8pm , su ɗan yi tattaki su zagaya unguwar zuwa 9pm sai su dawo gida , Ƙwarai yakaka take jin daɗin fitar tasu saboda yadda a kwanakin take jin nawin cikin kafafun ta duk sun ɗan kumbura , ga kwonkwason yana mata tsuku idan ta daɗe ," Tare suka fito da Rahima daga sashin su , Rahimar tana ta mitar Yakaka ta katse mata kallon TV da take ta dame ta akan tazo su fita ta raka ta motsa jiki ,"      Yakaka ni fa yau baza mu yi wani nisa ba , zamu dawo kin ga dai garin da sanyi ma , ga duk hazo ya rufe sama , ni ba dan kin nace ba ma wallahi yau baza mu fita motsa jikin nan ba duk ƙura ta bi ta shigewa mutum hanci ta sa mura ,"   Gyara zaman burmemen hijabin ta yakaka tayi tana murmushin jin daɗi domin tun basu yi nisa ba ma ta fara jin kafafun ta na warwarewa ,"      Ni kuwa Rahima daɗin yanayin ma nake ji , kiyi haƙuri kin san ba laifi na bane yaya dakta ne ya ce kar na dunga fashin fita motsa jikin ,"    Doctor hamza ne ya shigo ta ƙaramar ƙofar gidan jikin sa sanye da ƙananan kaya ya rufe bakin sa da hancin sa da abun tare ƙura ,"Mask ," Idon sa ya sauke a ƙan su lokacin da suke ƙarasowa ,"      Gaishe shi suka yi ya amsa musu ya ɗora da     Za'a je motsa jiki ko ? Da sauri Rahima ta tari numfashin sa , big bro daman an bar zuwa motsa jikin nan yau sai gobe , ji fa garin duk hazo wallah ,"        Rahima dan Allah kiyi haƙuri muje yakaka ta ce , tana marairaicewa ,"       Cuno baki Rahimar tayi taƙi cewa kome , "      Murmushi hamza yayi ,    Koma ciki abin ki Rahima yau an ɗaga miki ƙafa sai gobe ,      Da sauri Rahimar tayi juya tana dariyar murna , dan kar yace ta dawo ma har da ɗan gudun ta , ta ƙarasa shigewa sashin su , "    Ganin sa ya mayar kan Yakaka , wacce ta sunkui da kai tana wasa da hannun ta ,"       Noori   Ya ƙira ta    Na'am   Tace tana ɗago kan ta ta dube shi kafin ta sake sunkui da kan ," ba wani sanin ma'anar sunan tayi ba , ita dai tasan yakan ƙira ta da kalmar a irin lokuta haka da suke su biyu kaɗai !          Tunanin ta ya katse lokacin da ta ji yace mata ,   Bismillah mu tafi ,' ya buɗe mata ƴar ƙaramar ƙofar   Tare da shi zan tafi ? Ta tambayi kan ta lokacin da take sanya ƙafafun ta da ta cusa wasu ƴan takalman roba na mata ," kumburin da ƙafar ta ta tayi ya sa takalman suka ɗan kama kafar ,"     Ta ina-da-ina kuke bi idan kuka fito ?       Ta nan muke bi tace da shi da ƴar siririyar murya ,"     To yau ba nan zamu bi ba , zo mu bi ta nan , ya ce mata haka yana nuna mata hanyar da tayi baya wacce take da rangwamen mutane da hayaniya ,"    Ba musu ta bishi ,   Suka fara tafiya sannu ,sannu ,  rabin hankalin sa baki ɗaya na ga inda take sanya kafafun ta , "     Ɗan takaitatcen shiru ne ya biyo bayan fara tafiyar ta su ,"    Kafin Hamza ya lalubo hirar da yake ganin zata fi armashi ga yakaka ,"     Noori , ya ƙira ta ,"     Wanne suna kike tunanin zamu sawa baby ?      Yana hango lallausan murmushin da ya bayyana a fuskar ta da taimakon hasken fitulun bakin hanya, kafin ta ɗan sunkui da kan ta ,"     Nima ban sani ba yaya dakta , kawai duk wanda ka zaɓar mata ,"     Ɗan murmushi yayi kafin yace ai uwa ita ce mafi soyuwa ta zaɓarwa ƴaƴan ta suna ,     Ni mata ta duk ita zata dunga zaɓarwa yaran mu suna , dan haka mu fara da wannan babyn , ki tuno suna mai kyau da asali a addini da za'a sa mata , "   Kasaƙe tayi ita a dole tana son tuno da sunan ,!      Mama ? tace masa da sigar tambaya ,"     Mama!  shima ya maimaita yana kallon kwarar idanun ta ,"     Eh tace da shi tana sunkui da kai ," Toh kin samar mata da laƙabi ," ya furta hakan yana mai yi mata murmushin da ke bayyana sautin sa ,     Ita ma ƴar dariya tayi , tana jin yadda farin ciki ke mamaye mata rai , kafi ta ɗan cije baki a hankali tace na gaji ,     Yawata idanun sa yayi , nan ya hsngo wani ɗan tudun da aka yi da siminti a bakin hanya , domin zama ,      Muje ki zauna a chan yace da ita , Ƙarasawa suka yi ta zauna shi kuma ya tsaya daga gefe ," , ƙura ta taso tare da ƙasa ba shiri suka kare fuskokin su ,"     Sai bayan da ta lafa ya mayar kallon sa kan ta ," mask ɗin fuskar sa ya sanya hannu ya ƙunce , " a hankali ya miƙa mata ,"           Karɓi noori , ki saka ƙura tayi yawa ," kar ya cutar da ke ,"       Da hannu biyu ta karɓa , ta fara juya mask ɗin a hannu bata san yadda ake sawa ba ,"        Fahimtar hakan da yayi , yasa yace mata yana mai kwatantawa da hannun sa,     Haka zaki sa ,   Sake juyawa shi tayi ta fara ƙoƙarin ɗaura shi ba dai-dai ba ,"    Bani ki ga   Ya zare mask ɗin daga hannun ta ,  Zagayawa yayi ta bayan ta ya daidaita mask ɗin a fuskar ta tare da ɗaura mata shi , dai-dai kan hamcin ta zuwa haɓar ta ,"     Ya dawo ya tsaya , yana kallon fuskar ta , suna haɗa ido ta sunkui da kan ta tana jin wani irin yanayi marar ƙarfi chan a gefen ran ta ,"   A hankali ta motsa laɓɓan ta   Nagode ,! Bai amsa mata ba illa zura hannun sa da yayi a aljihun sa tare da kai kallon sa sama yana ganin yadda garin yayi jaa hazo ya lulluɓe sararin samaniya , Wani irin so da shauƙi mai ƙarfi yana fusgar sa bai ƙi ba suyi ta kasancewa anan daga shi sai ita ,     Shiru suka yi na ɗan wani lokaci kowa da abun da ke saƙawa cikin ran sa ,"  ya katse shirun da cewa    Zamu ɗan ƙara gaba ne ko mu koma gida ?       Mu koma gida yaya dakta , da rahima bama nisan haka ,"   Ok   Yace da ita . Suka kamo hanyar komawa gida suna tafe kakkarfar iskar juyin yanayi na shigowar Hunturu , na bugun su , rayukan su sun cika taf da mabanbanta tunaninnika ,! *****   Tun asubahin ranar juma'a Yakaka take jin ciwon baya da mara sai zirga-zirga take tsakanin banɗaki , ta gaza gane yanayin da take ji ,    Misalin ƙarfe tara Rahima tayi shirin ta zata karbo result ɗin ta na SSCE ,    Tayi musu sallama har tana tsokanar Yakaka ko zata raka ta ?    Uhum tace tana yamutsa fuska saboda ji da take kamar ciwon na ƙaruwa ,     Bayan fitar Rahima ya rage daga ita sai Falmata domin Hafsa ma tun bayan bikin Zainab ta tattara ta koma Hostel da zama baki ɗaya tana fuskantar jarabawar su ta ƙarshe , Doctor hamza kuma yayi kwanan asibiti , bai kai ga isowa gida ba , Karo na barkatai ta yunƙura da kyar ta tashi ta shiga banɗaki , sai dai a wannan karon ba tsugunno tayi ba wayar ta ta zaro daga cikin zanin ta ta kunna ta gami da fara neman layin samy baby tayi mata flashing , Tana addu'ar Allah ya sa ta tashi a bacci yanzu , domin wayar ma gaf take da kashe kan ta chajin ya kusan cimma ƙarshe , Ta kuwa yi sa'a  cikin ƙasa da mintuna biyu sai ga ƙiran samy baby ," Hello yaks ya Kike ? Bani da lafiya anty samy bayana kamar zai ɓalle nake ji ,"         Miƙewa samy baby tayi daga kwance ,"     Yaks ko dai haihuwar ce ?   Da ƙyar take magana saboda ciwon da take ji yana sake tsungulin ta ,"    Inajin ita ce anty samy  daman haka haihuwar take da ciwo ??   Gintse dariyar da take taho mata samy baby tayi , sannu yaks , ki tabbatar dai bamu samu kuskuren aiwatar da nufin mu ba , yanzu zan je harabar asibitin da kike awun na tsaya da mota ta , na jira zuwan ku kin ji ko ?    to tace tana sauƙe wayar daga kunnen ta ,"   Falo ta dawo tana cigaba da murƙususu , tare da nishi ƙasa-ƙasa     Tsai Falmata tayi daga barin tilawar Al-qur'anin da take yi cikin suratu,"Duhaa,'     Da sauri ta miƙe tana laluben inda take jiyo nishin Yakaka ,"   Yakaka ,Yakaka , Yakaka ,nydan3 ? Aiyii waaz3n ? Manan3 Yakaka , Aiyii ?      Buguwar da tayi da kujera ta faɗi shi yasa Yakaka wacce take durƙushe daga bayan kujerar rarrafawa ta fito , tazo ta kama hannun Falmatan , wacce bata kula da zafin da ɗan yatsan ta yake ba wanda ya fashe yana tsastsafo da jini , " Bani da lafiya Falmata , yakaka tace da ita da wata ƴar murƴa chan ƙasa , tana mai zamewa ta kwanta gami da ɗaura kan ta akan cinyoyin Falmatan Wani irin ciwo take ji marar misaltuwa tana jin kamar wani abu ya tokare ta , da zata iya zata sanya hannun ta zaro shi ," Ta gaza rarrashin falmata wacce ruwan hawaye ya ɓalle a idanun ta , tana iya hango tsoro tare da matsanancin firgicin da ya cika ƙwarar idanun Falmatan , nan take taji wani yanayi ya karci ran ta marar daɗi , A gajiye ya shigo falon bayan fitowar sa daga sashin mahaifin sa inda ya fara yada zango a tun shigowar sa gidan ,    Tana maƙale a ran sa shiyasa ya gaza wucewa yaje ya kwanta ya huta kamar yadda gangar jikin sa ke muradi , sai da ya biyo domin ganin fuskar ta ,        Nishin ta tare da sautin kukan Falmata ya fara ji kafin idanun sa su hango masa su a tsakanin kujera , da wani taku da yafi dacewa a ƙira sa gudu ya ƙaraso wajen , kallo ɗaya yayi mata ya fahimci halin da take ciki ,   Rahima , da hafsa har ma da zainab waɗanda basa gidan su ya fara kwalawa ƙira , saboda ruɗewar ganin ta a ciwo , "    Bai ƙarasa jin Falmata wacce take mar bayani cikin muryar kuka akan , su Rahima basa gidan fa ," ya fita da gudu yayi sashin sa ya sanya mukulli ya buɗe , kai tsaye wardrobe ɗin da ya nufa ya ciro manyan ledoji ukun da suke ɗauke da tambarin ,"Today's,'  da suke shaƙe da kayan haihuwa zuwa kayan baby da duk wani abun da za'a iya buƙata a yayin sabuwar haihuwa ya tanada ,hatta dogayen riguna biyu da mai jego zata sa a jikin ta bayan haihuwa , zuwa dogon wondo har da panties  duk ya saya ya adana , da babu wanda ya san hakan daga Allah sai shi ,,' Da gudu ya koma gidan bayan ya zuba kayan a bayan mota , Fatima kama ta mu tafi asibiti ,     Toh tace tana mai kamo Yakaka da kyar suka miƙe tsaye , , da kyar Yakaka take cira ƙafa jin yadda cikin ya dunƙule guri guda , baya da ƙugun ta kuwa , ta tabbatar sun ɓalle, bakin ta ya rufu gum , ba un ba un-un . Da gudu ya jaa motar kasancewar akwai rangwamen ababan hawa ya sa basu ɗauki dogon lokaci ba suka iso asibitin yayi parking kusa da wata brown ɗin mota matrix," Da sassarfa ya shiga ciki , sai ga shi sun dawo tare da nurses biyu da wasu ma'aikatan asibitin su ma biyu , Suka kama yakaka suka ɗora ta akan wheelchair , suka tura ta zuwa cikin asibitin da matuƙar sauri , Doctor Hamza da Falmata suka bisu a baya da hanzari ," Duk abun da suke akan idon samy baby wacce take cikin motar da take gefen ta Doctor Hamza , ta riga su zuwa wajen kamar yadda ta al'ƙawar ta , sake gyara kishingiɗar ta a jikin kujerar motar tayi , cikin ran ta tana addu,"ar kome ya tafi yadda ta tsara ,! Da hawa gadon ɗakin haihuwa da haihuwar Yakaka duk abune wanda ya faru a tsakanin mintoci talatin ," Haka kuma baza ace anyi haihuwa a ɗakin ba saboda jaririyar kukan farko da tayi na zuwa duniya tun daga nan ta lalubi ɗan yatsan ta ta danna a baki tana tsotsa a hankali , tayi luf kamar mai bacci , Har aka ɗauke ta aka shige da ita wata ƴar kofa inda aka tafi duba lafiyar ta , Yakaka kuwa wacce take jin ta sawai kuma garau , tamkar ba ita bace wacce take jin ciwo kwatankwacin na mutuwa mintoci talatin da suka wuce , sai tsokanar ta tare da jaan ta da hira likitar da ta ƙarbi haihuwar ta take yi , tana kuma ƙara jinjina mata akan namijin ƙoƙarin da tayi wurin haihuwar , sam Yakaka bata da raki irin na wasu matan musamman haihuwar fari ta yadda za'a ji idan sun zi haihuwa suna ta faman ihu tare da sambatu marasa alfanu ,! Hankalin ta baki ɗaya baya ksn likitar , ys tafi ga son sanin ya suke akan tsarin su , ita dai babu wayar a hannun ta a halin yanzu bare ta kira samy baby , bata fatan ace shirin su ya ruguje domin ta riga ta ƙwallafa son cikar burin ta a ran ta , shiyasa take ƙoƙari gurin kaucewa duk wani abun da zai sa mata tarnaƙi ya sa ta fasa nufin ta , hakan ya sa ko jaririyar bata duba ba,  da tun da ta iso duniya bakunan nurses tare da likitar da ta karɓi haihuwar bai gajiya ba gurin faɗin ",Masha Allah , Tubarakallah ," Tana jin yadda suke amfani da mabanbantan kalmomi gurin koɗa kyaun jaririyar , "    Har ɗaya daga ciki take faɗin ita tun da take karbar haihuwa bata taɓa ganin mai kyaun wannan babyn ba Tubarakallah ,"     Likitar tana gama gyara ta da tabbatar da lafiyar ta , ta wanke hannuwan ta ta leƙa waje , inda  Doctor Hamza yake ta kai kawo Falmata kuma take zaune daga kan kujerar da aka tanada domin zaman jira ,"   Yana ganin Doctor ta nufo shi shima ya ƙara taku zuwa wajen ta ," Da murna da fara'a take sanar da shi cikin harshen Turanci , matar sa ta haihu lafiya ta haifi kyakkyawar ɗiya mace , a halin yanzu bazai jima ba za'a fito da uwar zuwa ɗakin hutu daga bisani kuma idan an gama duba Lafiyar jaririyar za'a kai ta wurin mahaifiyar ta , " Wani irin farinciki yake ji yana huda shi tamkar dai matar sa ce ta haifa masa ɗiyar sa da gaske bakin sa yaƙi rufuwa sai kalmomin godiya yake jerawa ga ubangiji, " Juyawa yayi lokacin da likitar take komawa ciki , ya nufo Falmata wacce bata kai ga fahimtar me suka tattuna shi da matar da ta ji tashin muryar ta ba ,"   Kallon ta yayi yana aina ya zama dole ya samo mai taimakawa yakaka a halin yanzu da ya san jikin ta ba ƙwari ,kuma haihuwar farko ce tana bukatar wani babba a kusa da ita  Falmata , yarinya ce kuma miskiniya baza ta iya bawa yakaka taimako ba a wannan gaɓar ,"    Amne ita ce ta faɗo masa a rai , ya lura tana son yaran musamman ma Yakakar , kusan koyaushe suka yi waya sai ta tambaye shi game da yaran , dan haka ya san baza ta ƙi ba idan ya nemi ta kula da yakaka ,"    muryar sa wasai yace da ita ,       Fatimah , ki jira ni zan je na zo da Amne yanzu , Yayar ki ta haihu , kar ki je ko'ina ,    bai jira cewar ta ba ya wuce da sauri yana duba agogo , saboda gudun lokacin juma'a ya shigo , " ya bar Falmata da tarin farinciki cike fal da zuciyar ta , tare da son sanin a wanne hali yayar ta da jaririyar su suke ciki a halin yanzu?? samy baby tana ganin tashin motar Doctor hamza , da fitar shi daga asibitin ta fito daga cikin motar ta gami da gyara zaman hijabin kan ta bayan ta ɗauko wata babbar leda baƙa da flask ɗin ruwan zafi ta nufi cikin asibitin da ta riga ta zo shi sau dayawa ta yawata a ciki ta san kan shi tare da hanyoyin cikin sa ," Ta gaban Falmata ta zo ta wuce ta ƙarasa daf da kofar ɗakin haihuwar ta tsaya , tsayuwar mintuna uku tayi jal , aka buɗo kofar ɗakin gami da turo Yakaka akan kujerar ɗaukar marasa lafiya ,"    kallon kallo suka yiwa juna kafin su sakarwa juna murmushin da yake bawa nursese ɗin tabbacin sanayya a tsakanin su biyun , Yakaka ta sunkui da kan ta ƙasa   Ba tare da sun cewa juna ƙala ba aka cigaba da tura Yakaka samy baby na take musu baya suka zo suka gitta ta gaban Falmata dai-dai lokacin hawayen da suke idanun Yakaka suka fara sauka yif-yif , tana hango ƴan kyawawan kafafun falmata dusu-dusu , sakamakon ruwan hawaye da ya cika idanun ta , Aka wuce da ita zuwa ɗaKin hutun ,samy baby da sai da suka shiga ɗakin tayi magana ,"    ta kama yakaka ta kwantar ta a kan gado tana ta faman jera mata sannu ,"    Sannu ƙanwa ta , sannu kin yi kokari ,!    Ah tayi kokari sosai cewar nurse ɗin da take ƙoƙarin ɗaurawa yakaka  ƙarin ruwa ,"     Ƙanwar ki ce ko ? Ina mijin nata ?    ai ga shi kuna kama , farar fatar ku ɗaya , ki kula da ita zan je na zo da baby , ki haɗa mata tea mai kauri sosai !     a jimlace samy baby ta amsa da   Toh   Lokacin da nurse ɗin take barin ɗakin ,"   Tana fita samy baby ta miƙe , Tashi tashi mu tafi Yaks , bamu da isashen lokaci ,"   Da wani irin yanayi a fuskar yakaka ta miƙe zaune lokacin da samy baby take cire mata ƙarin ruwan da aka maƙala mata ,"    FALMATA tace tana mai share ambaliyar ruwan hawayen da ya zubo mata ,"   Meye haka yaks ? Zaki ɓata mana shirin mu ne ? Anty samy Dan Allah ki bari mu tafi tare da Falmata ,     No no no yakaka kar ki ɓata mana tsari idan kin  haƙura kin fasa zuwa wajen yarima ɗin ne ni sai nayi tafiya ta , daman taimakon ki zan yi kamar yadda na faɗa miki tun farko , shi yace na zo na kai ki gurin sa ," idan kin fasa sai na koma na faɗa masa ke yanzu bakya son shi kin samu wanda ya fi shi ,    share hawayen ta tayi da bayan hannun ta ,"    Toh ki barni naje na faɗa mata kome , na faɗa mata kar ta damu zan je muyi aure da baban baby na dawo na ɗauke su ita da baby , bana son Falmata ta samu matsala sakamakon barin ta da zan yi ba tare da sallama ba , nasan zuciyar Falmata baza ta ɗauki rashi na irin haka ba , Falmata Bata da kowa bayan ni ,   mtss samy baby ta jaa tsaki lokacin da ta sunkuya ta ɗau ledar da ta zo da ita ,"     yaks ni kin ga bari na tafi tun da duk tsawon lokacin da muka ɗauka muna tsara yadda kome zai kasance yau da ranar ta zo kin rusa kome da kan ki , sai kiyi ta zama , cikin rayuwar da gaba kaɗan zaki yi danasanin taɓa wanzuwar ki cikin ta idan kika haɗu da kaidi tare da masifar da take yanyame a cikin ta ,   Ni kin ga tafiya , tace tana nufar bakin kofa ," Wani irin tsalle zuciyar yakaka take , auren Youssouf babban nasara ne tare da cikamakin duk wani farin ciki na rayuwar ta ,"    Ki tsaya anty samy , na YARDA ZAN BIKI KI KAI NI WURIN BATURE KAM SULUM ,"   Wani shu'umin murmushi samy baby tayi kafin ta dawo cikin hanzari ta buɗe ledar hannun ta tare da zaro wasu manyan hijabai har ƙasa guda biyu ,      Ta zurawa yakaka ɗaya ita ma ta sauya na jikin ta ta kamo hannun yakaka , wacce duk take a ruɗe a gigice , cikin rasa gane takamaimai a yanayin da take ciki , "    ki saita tafiyar ki mai kyau kin san ta gaban a ɗakin haihuwar zamu zo mu wuce  , samy baby tace da ita haka lokacin da suke barin ɗakin ,"        Ta gaban ɗakin haihuwa suka wuce da ya kawo su har gaban Falmata wacce take zaune jugum har lokacin idanun ta kafe guri ɗaya ," duk jikin ta yayi sanyi haka kawai take jin bugun zuciyar ta na sauyawa tare da tsikar jikin ta da take ta tashi akai akai , kwalla na taruwa a gurbin idanun ta ,    Da hannu Yakaka ta toshe bakin ta domin hana kukan da take yi fitowa sarari yayin da ta runtse idanun ta gam ,  da taimakon hannun ta da samy baby ta matse tsam suka wuce ta gaban falmata ,     Wucewar su ya zo dai-dai da zubowar ƙwallar idanun Falmata , sannan kunnen ta na jiyo mata tamkar takun kafafun Yakaka suna nisa da ita ,"     Yakaka ki fito na gan ki    ta furta a sarari , tana mai saita idanun ta inda kamar take jiyo takun kafar Yakakar Sun kusa fita a kan doguwar hanyar suka tsinkayo kukan jaririyar da ya karaɗe wajen ,      Chak yakaka ta tsaya , A sarari ta furta MAMA , tana mai waigawa da sauri , daga inda take tana hango jaririyar a naɗe cikin wani ɗan kyakyawan baby pink ɗin mayafin da aka naɗo ta ciki , sai wutsil wutsil take da hannu , ga alama hakurin ta ya ƙare ,tana neman abincin ta idanun ta ta sauke akan Falmata wacce ta kafe hanyar da suke da ido , idan ba gizo idanun ta ke yi ba tana iya hango kyallin hawaye a idanun falmata , Wani abu ta ji ya yanki zuciyar ta , cikin ta ya ƙarta , ta ji kamar ta zura da gudu , ta rungumi waɗannan bayin Allah guda biyu da take shirin bari cikin maraici ,"    bata yi aune ba ta ji samy baby ta fusgi hannun ta lokacin da ake shigewa da babyn hanyar ɗakin da aka bata , Falmata tana mai juyar da kan ta inda take jiyo tashin kukan jaririyar da take jiyo shi da wani yanayi mai girma da yake huda zuciyar ta yana taɓo ƙasan ran ta," Da wata irin dusashiyar muryar da kuka yaci karfin ta take kiran sunayen su su biyu lokacin da samy baby take jaan hannun ta zuwa gurin motar ta ,"   FALMATA , MAMA , Tana zuwa ta buɗe mata gidan baya da taimakon ta ta shiga , ta zagayo ta buɗe mazaunin direba ta shiga , tana jin yadda tata zuciyar ma take yin rauni da matsanancin tausayin rayukan da yake lulluɓe ta ,tana tuhumar kan ta Anya Anya kuwa ita SAMIRA ta kyauta ??? Da gudu ta bar hsrabar asibitin ta fito kan babban titi , ta miƙa hanya sosai ta nufi kwadaben barin gari , kasantuwar daman da shirin ta tsaf , sai kawai ta ɗaɗɗaga gilasai lokacin da ta hau kan babban titin da ya nausa ya nufi wajen gari , sashi na ran ta na ƙarfafar ta akan ƙudirin ta , a hankali yakaka ta sauke hijabin da ta ja ta rufe fuskar ta baki ɗaya da shi ta ɗaura jajayen idanun ta da suka rine suka kumbura hatta fuskar ta tasa ta saita ganin ta akan titi tana kallon manya bishiyoyi da ƙananun dazuzzukan da suke kusa da gari ," zuciyar ta na wani irin ƙuna , ƙuna mai tsanani , tana jin ta empty , tana jin ta kamar tana kan guguwa tana walagigi da ita tana jin tamkar ta rasa kome da kowa , tana jin tamkar tayi KUSKURE MAFI GIRMA A RAYUWAR TA .! A hankali ta maida kan ta jikin tagar motar ta kwantar tare da runtse idanun ta , zuciyar ta na dawo mata da hoton Halin da ta bar FALMATA DA MAMA a ciki , kunnuwan ta na amsa kuwwar kukan JARIRIYAR TA ... WAI     Wai        Wai Assalamu Alaykum kowa da kowa , ina gaishe ku tare da fatan Alheri , nasan kun yi dogon jira na tsawon sati biyu cif yau ' da fatan zaku dunga min uzuri , domin da ace ɗaya daga cikin ku ya san tarin aiyukan dake jibge akai na wallahi da babu mai yin ƙorafin rashin ganin cigaba akai akai , duk da haka zan ji daɗi idan ku ka cigaba da min uziri , ɗan adam a koyaushe yana buƙatar ɗaga ƙafa tare da bada dama !!   Nagode kwarai da yadda ku ke bibiyar rubutuna , tare da ku da taimakon ku rubutun har ya miƙa ya haka ,, ina fatan zaku cigaba da bibiya ta har mu cimma matsaya ," kofar shigar da ƙorafi ko gyara tare da ra'ayoyi a buɗe take a gare ku , kai tsaye zuwa gare ni , zan ji dadi kuma zan yi amfani da shawarwarin ku muddin bai saɓawa ainahin tubalin ginin labarin ba .   Nagode !                         [6/24, 10:59 AM] +234 701 013 7848: Mafari ..... ( Hargitsin Rayuwa ) umm'muaz 27 Da sauri Doctor Hamza yake tafiya ," Amne na bin bayan sa , lokacin da suke kutsawa cikin asibitin , bayan sha da kyar da suka yi a cikin cinkoson ababen hawa da ya fara haɗuwa akan titi sakamakon kusantowar lokacin sallar juma'a ," Sai dai tun da ya dosa bakin ɗakin haihuwar taron mutanen da ya gani kama daga likitocin asibitin zuwa kan nurses da securities ya sa shi rage takun sa ,"   Maganganun da ya ji suna faɗa cikin harshen turanci tare da kama sunan AMINA DILMARI shi yasa shi zabura ya kutsa tsakanin su ,     What's happening/ Me yake faruwa ? yace da su cikin wata irin muryar ,   Calm down sir , Babban likitan da asibitin yake mallakin sa yace yana kamo kafaɗun doctor Hamza , Muje office muyi magana ,"  zame kafaɗun sa doctor Hamza yayi lokacin da yake fuskantar likitan ,    Ina patient ɗina ? Yace da buɗaɗɗiyar murya , "    Shiru likitan yayi ,"   Wani irin bugu zuciyar Hamza take kamar zata fito waje ," kasancewar sa cikakken likita yasan yanayin da suke yi a duk lokacin da suke son sanar da mutanen marar lafiya wani mummunan labari game da marar lafiyan su,!    Ta mutu ? Ya tambaya yana jin yadda zuciyar sa ke matsewa da tasowar ɗacin kalmar har akan harshen sa ," Da sauri likitan yace    Bata mutu ba amma zai fi kyau idan muka je nayi maka bayani a nutse.   A sanyaye Doctor Hamza ya bi bayan likitan bayan ya nunawa Amne wurin zama a gefen Falmata wacce tayi zugui idanun ta sun yi jaa sakamakon hawayen da take ta gogewa kan rashin sani halin da ƴar uwar ta ke ciki har kawo wannan lokacin , Mun rasa gane yadda akayi ko dalilin da yasa matar ka tare da ƴar uwar ta suka bar asibiti kuma suka bar ƴar jaririyar ta ba tare da mun sallame ta ba , sannan Alamu suna nuna kai ma baka san sun tafi ba ,"      Ɗan tsayirtawa likitan yayi yana nazarin fuskar doctor hamza wanda yayi saƙare yana kallon sa , kamar dai bai kai ga fahimtar bayanin da yake masa ba ," ɗan ƙwanƙwasa bakin biron hannun sa yayi akan ƴar takaddar gaban sa,"      Idan har an tabbatar tana gidan zamu iya sallamar ku tare da jaririyar domin ayi gaggawar sadata da mahaifiyar ta domin ta shayar da ita nonon farko ,"    Cikin jirkitattacen kallo Doctor hamza yace wacece ta gudu tare da ƴar uwar ta suka bar jaririyar ?     Tamkar dai sam bai ma fahimci bayanin da duk likitan nan ya masa ba ,"     Ba kai ne mijin AMINA HAMZA DILMARI BA ?    Maimakon ya amsa sai ya miƙe tsaye ,    Kana nufin ita ce suka gudu tare da ƴar uwar ta ?    A taƙaice likitan yace Haka muke zato domin an duba duk inda yakamata cikin asibitin nan ba'a gan su ba , sannan masu tsaro/securities sun tabbatar mana da sun ga fitar mata biyu farare sanye da hijabai sun hau.....    Ankarar da yayi doctor hamza ya juya daga ofishin ya sanya shi miƙewa ya biyo shi ,     Wurin da ya bar Amne da Falmata nan ya dawo ,"   Fatimah , kun haɗu ke da yayar ki ? Da sauri ta ɗago kan ta ! Bamu haɗu ba Yaya dakta har yanzu ba'a kai ni inda suke ba ita da baby , ko basu da Lafiya ne ? Dan Allah ka kai ni wajen su ,'!    Wani gumi yaji yana tsatsafo masa daga illahirin ƙofofin gashin jikin sa ,"   Amne ta taso ta matso kusa da shi ," Ina mai jegon ne ?   wai ba'a gan ta ba yace da wata irin murya chan ƙasa , Amne dake kusa da shi kaɗai ta iya jin mai yace   Wanne irin ba'a gan ta ba inji amne ,'   Lokacin da likitan ke sake ƙarasowa tare da wasu nurses da wasu securites ,       Kuyi haƙuri sir , a fara duba gida ko suna chan , domin tare da ƴar uwar ta suka fita ,"    Wata kakkarfar tsawa doctor hamza ya yiwa likitan ,    Ka daina cewa tare da ƴar uwar ta suka fita , "    Ga ƴar uwar ta nan , ya juya yana nuno musu Falmata wacce ita ma ta miƙe tsaye tana rarraba ƙwayar idanun ta da son sanin meke faruwa?   Ita kaɗai ce ƴar uwar ta , ya zama dole ku nemo ta  , ba gudu tayi ba sace ta aka yi , Yakaka baza ta gudu ta bar Fatimah ƙanwar ta ba baza ta gudu ta bar baby mama ba , noorie baza ta min haka ba , ya ƙarashe da rawar murya yana jin yadda zuciyar sa ke cika da tsoron tabbatuwar hasashen mutanen asibitin ,"    Sir kayi haƙuri amma matar ka ba sace ta aka yi ba ita da ƙafafun ta suka fita tare da wacce tace sister nata ce , bayan tafiyar ka matar ta zo , tanan muka wuce da ita , wannan yarinyar da kace ita ce ƴar uwar ta tana zaune a wajen bata nuna ta san yarinyar ba basu mata magana ba su duka biyun , sai da muka je ɗakin , suka yi magana , kuma lokacin da nake fitowa da baby domin kai ta wurin mamar ta naga bayan wasu mata biyu suna fita , ina hasashen su ne , domin su ne kaɗai matan da aka ce an gani sun fita da hijabi tsukin awannin nan ," ka zo ma na nuna maka shaidar flask ɗin ruwan zafin da matar ta kawo , har yanzu yana ɗakin !,    Cewar wannan nurse ɗin da ta kai yakaka ɗakin hutuwa ," Bai ce ƙala ba ya bita a baya zuwa ɗakin , anan ya tadda flask ɗin da ta ambata tare da wata ɓakar leda da sauri ya ɗauki ledar ya buɗe ,    Babu kome a ciki sai hijabin yakakar wanda ta zo da shi asibitin ," hajabin da yayi wa farin sani domin shi da kan sa ya saya mata su guda biyar mabanbantan launika .     Shiru ne ya ratsa ɗakin ,"    Doctor hamza yayi shiru kan sa a sunkuye da alama ya zurfafa cikin tunanin me yake shirin faruwa ne ? Da gaske ta gudun ne ? To meyasa zata yi haka ?Anya tana cikin Hankalin ta ? Ko dai gida suka koma tare da RAHIMA ? Idan ba haka ba yaran wa suka sani ? Ina za ta ? Basu da kowa ƴan gudun hijira ne .    Ina baby ??   Da sauri babban likitan yace a je a zo da baby , yana fatan Allah ya sa wutar masifar da take son kunnuwa masa a asibiti kar ta kai ga ruruwa har ta ɓata masa sunan asibiti .    Nurse ɗin ta dawo tare da Baby wacce ɗumin tsaftatatcen ruwan da aka cika mata ciki da shi ya sa ta fara bacci ,"    Miƙa masa ita aka yi ya karɓe ta , bai ce ƙala ba ya jiyo ya fito daga ɗakin ,"    Wajen da ya bar Amne da Falmata nan ya dawo    Mu tafi gida yace da su ,! Ita Yakaka ta koma gida ne  ?  Meyasa ta tafi ta bar baby wanne irin shirme ne wannan ?       cewar Amne ,   Yaya dakta Ina yakaka ɗin ? Bata da lafiya ne ?     Shiru yayi bai amsa musu ba , ya tsinci kan sa cikin ruɗani ,    Kai tsaye gidan Amne ya nufa da su , Amne riƙe da jaririya tare da Falmata suna baya a zaune shi kuma yana jaan motar ,"     Takamaimai bai san tunanin me yake ba , abu ɗaya ne yake fata , shine ya je gida ya tadda ta tara da Rahima sun koma gida , wani tsoro-tsoron tabbatuwar bata gidan ya sa shi kin ɗaga waya ya ƙira rahima yafi so yaje gidan da kan sa ,"   Ku shiga gida Amne zan je na duba ta wataƙila sun koma gida ita da Rahima , ya furta hakan ba tare da ya bari sun haɗa ido da Amne ba wacce take kallon sa     Wai me su likitocin suka ce maka ne ? Cewa suka yi sun tafi gida ita da rahima ?      Waigowa yayi ya dube ta , da hannun ya nuna mata Falmata tare da yi mata Alamun roƙon tayi shiru ta bar maganar tukun , " duba da yadda a halin yanzu ma Falmatan duk a hargitse take tunda suka hau motar bata ce uffan ba sai faman share ƙwalla take tana jaan hanci ,"   Fita yayi ya buɗe mata kofar motar ,   Amne bata sake magana ba ta kamo hannun Falmata suka fito tare da jaririyar zuwa cikin gidan ta ," Komawa yayi cikin motar ya zauna ya ɗora hannuwan sa bisa kan Steering motar yayi shiru , zuciyar sa na kai kawo ,"    Ƙwanƙwasa gilashin motar da aka yi shi yasa shi ɗago kan sa ya sauke akan matashiyar yarinyar da ke tsaye a jikin motar sa ,"     Murmushi tayi masa ya ga lokacin da bakin ta ya motsa alamun gaisuwa ,"    Gyaɗa kai yayi kafin ya juyar da kansa ya fara ƙokarin tashin motar ,"   Zaton sa irin ƴan matan unguwar ne take gaishe sa ,"   Ƙara ƙwanƙwasa motar tayi da ɗan ƙarfin ta , tana masa magana ,"   Tsaki ya jaa mai sauti kafin ya sauke gilashin motar ,"       Kalaman ta suka doki kunnuwan sa da yasa ba shiri ya zuro kafafun sa wajen motar gami da miƙewa tsaye ,"    Me kika ce ?    Ɗan matsawa tayi baya kaɗan tana wani guntun murmushi tace    Yakaka ce ta aiko ni , tace na sanar da kai ita ta tafi Abuja wajen Baban Ƴar da ta haifa domin a ɗaura musu aure , dan haka kar ma ka sha wahalar neman ta bayan auren su nan da watanni kaɗan idan sun gama moneehmoon zata dawo kuma tace wai......      Marin da ya kwashe ta da shi ya hana ta ƙasara zancen ta ,sai da tayi taga-taga ta sunkuya , tana ɗagowa ya sake ƙara mata wani ,"      Shoƙo gelen wuyan ta yayi ya maƙure ta , "    Ina kuka kai ta ? Ke da su waye kuka haɗa baki kuka sace ta ? Zaki nuna min inda take ko sai na sada ki da jami'an ƴan sanda sun lallasa ki ,"    Idanun YAGANA sun fiirfito tace wallahi gaskiya nake faɗa , yakaka ƴar uwa ta ce tare muka zo garin nan , tun a sansani muke tare , cikin shege tayi madam ɗin da muke yiwa aiki ta kore ta , shine yanzu bayan ta haihu suka haɗa baki ita da uwarɗakin ta ta gudu zata koma wajen shi suyi aure ,"    Angaje ta baya yayi ,"   Ƙarya kike yi ,"ƙarya ne noorie ƙaramar yarinya ce bata isa shirya wannan wasan ba , ban yadda da ke ba , dole zaki faɗi gaskiya idan kika ji duka a wajen hukuma , wayar sa yake ƙoƙarin zarowa lokacin da ya ji tace ,"    Idan ƙarya nake bari na ƙira uwarɗakin nata ka ji muryar yakakar ma wallahi ,"    Bata saurari amsar da zai bayar ba ta danna ƙiran number samy baby bayan ta saka wayar a hands free , wacce daman jiran ƙiran yagana take , "     Dan haka ta rage gudun motar tare da gangarawa gefen hanya tayi parking sannan ta ɗauki wayar ,     Hello Doctor tace da shi , bata jira amsa sa ba ta juya harshe zuwa turanci ,"inda take cewa    Nasan zaka yi mamakin yadda abubuwa suka faru , wanda a zahiri ba wani abu bane na ban mamaki duba da yadda idanun ka suka makance basirar ka ta toshe , zuciyar ka kuma ta mace akan son yarinya yakaka , ita ma haka tata zuciyar ta mace , ta samu toshewar basira tare da makancewa cikin son wanda zuciyar ta ta zaɓa har ma ta daɗe da mallaka masa ruhi tare da gangar jikin ta baki ɗaya , " ba wani bane wannan illah uban ƴar ta wanda soyayya ta sa ta bashi kan ta , har kuma ta zaɓi rabuwa da ƴar ta tare da ƙanwar ta saboda ta tsira da shi , kana mamaki ko ? Ko kuwa zato kake ƙarya ne ," tunanin ka shiri ne koh ?  To bari ka ji kasan daman waƙa a bakin mai ita yafi daɗin sauraro ," Juya harshe tayi ta dawo hausa , Yaks , Yaks ,    Ke yaks    A hankali ta ɗago kan ta da yake bala'in sara mata ta kalle ta da idanun ta da suke cike taf da hawayen tausayin kai ," duk da daman tana jin ta tana waya da turancin da ba fahimtar sa take ba , ba bacci take ba ,    Na'am anty samy ," Ga Yariman naki ko kuwa me ma kike ƙiran masoyin naki ??    Cikin sanyin muryar tace Bature kam silum ?   Eh shine akan wayar riƙe kuyi magana ,"    Anty samy kice masa kawai ina zuwa zan zo wajen sa zaki kawo ni , bana jin yin dogon magana , zuciya ta ciwo take min ban san a wanne hali Falmata take ciki ba ,"      Cije baki samy baby tayi tana hararar yakaka da ta lura tana son ɓata mata shiri ,"    Bana son kinibibi bake kika yadda zaki wajen nasa ba ko na mayar ki ne ?    Shiru tayi bata ce e ba ko a ah   Karɓi wayar ki masa magana ya ji ki ,"    Alo Bature kam silum , gani nan zan zo wajen ka , anty samy zata kawo ni , amma gobe nake so mu dawo mu ɗauki su Falmata da mama , sai muyi aure mu zauna tare da su Dan Allah bazan iya zama babu su ba ina son ku ku duka sosai ka yadda koh ?      Ƙarɓe kan wayar samy baby tayi tana murmushin nasara , ta koma turanci     Sauran ƙarin bayanin da zai iya gamsar da kai yana cikin kayan ta tare da wayar ta da ta bari a gidan ku , da fatan zaka rungumi haƙuri , ka nemo matar da zata iya mallaka maka ruhin ta tare da sadauƙarwa irin wanda yakaka tayi ga masoyin ta ," idan kunne yaji .... ? Tace da shi tana sauke wayar a kunnen ta tare da latse ta ta kashe ta tada motar tana fincikar ta da ƙarfi ..    Tun kafin ta gama furto zantukan ta yake jin wani abu mai kama da hayaki yana lullube masa zuciya wani irin ƙaƙƙarfan kishi da tsanar yarinyar suka tarwatsa masa rai da ya sa jin kan sa na juyawa , tabbas ta yaudare shi , yaudara mai girma , ta ha'ince shi ta kuma butulce masa ," Amma anya , toh Anya gaskiya ne anya ba tursasa noorie aka yi ba ,! Anya tana da wayo tare da hikimar yin mummunar yaudara irin haka , sashin zuciyar sa da soƴayyar ta tayi ƙarfi ta kafa rassa ke son kawo uziri ke son bata kariya ke son wanke ta , ke son fidda zargi a tsakani , Bai bi ta kan yagana ba ya faɗa cikin motar sa ya jaa da ƙarfi gami da nufar gida domin ganin shidar da aka ce akwai , Gyara gelen ta tayi wanda ya cukurkuɗe , kafin ta ce     Wannan Banzan har mari na yayi akan wata banzar sokuwar yakaka , oho dai a yau zan yi kwanan farin ciki sanin cewa yakaka tayi nisa da garin maiduguri baki ɗaya , " babu ranar dawowa !   Kai kuma marin nan wallahi bashi ka ɗauka , zan rama shi ta wata hanyar da baka yi zato ba a kuma lokacin da baka yi tsammani ba ,     Wucewa tayi ta kutsa cikin unguwar da daman take ta su , tana hararar gidan Amnee inda take da tabbacin ciki jinin Yakaka suka yi bigire ,"     Cikin ran ta ta fara saƙa da mummunar zaren da zai iya zargewa har da ita ,"      Kusan da gudu-gudu ya shiga sashin su Rahima bai ko tsaya rufe ƙofar motar sa ba ,"    Rahima , Rahima , Rahima yake ƙwalawa ƙira ,   Da gudu ta fito daga ɗakin ta tana ƙoƙarin ɗaura ɗankwalin ta ta shirya tsaf domin zuwa asibitin wajen su Yakaka , jin shirun yayi yawa tun hantsi har ga shi ƙarfe uku ta ƙarato.ta tabbatar zuwa yanzu ta haihu ," Na'am big bro , ina su Yakaka ya jikin nata ? Ta haihu ,? Me muka samu ? Ina wajen kayan su yake ?  Yace da ita haka idanun sa sun kaɗa ,"   Kayan su wa ?   Fatima .   yace da ita Wani abu zan ɗauko maka ?  Me zan ɗauko maka big bro ta haihu ko ? Me ta haifa ? Ina wajen kayan su nace miki , ya daka mata tsawar da ta firgita ta ,   Da hannu ta nuna masa ɗakin su Yana cikin wardrobe ,   Kayan yayar fatima nake nufi Duk kayan su a haɗe suke big bro , ta furta hakan tana karya wuya , ran ta cike taf da jimamin abun da ya hatgitsa musu ɗan uwa haka ,"      Watsi yake da kayan su yana hautsinawa , har zuwa lokacin da idanun sa suka sauka kan ɗan ƙaramin hoton tare da agogo haɗi da damin kuɗin niger da suke chan ƙasan kayan ta ,"    Zuciyar sa na bugawa ya ɗauki ƙaramin hoton fasfo ɗin gami da kai idanun sa kan fuskar kyakkyawan bamarɗen ingarman saurayin da bai fi sa'an sa ba jikin sa sanye da kakin soji na ƙasar niger , hoton a zamunance yake babu wani alamun tsufa ,"   Tabbas shine ba tantama kome gaskiya ne , ya aina haka cikin ran sa lokacin da yake sake jujjuya agogon da rannan ya gan shi a hannun ta , tace masa na BABAN ta ne , tunowa yayi da ranar da ta nace ya kai ta bakin kasuwa , tace cikin kayan ta akwai hoton BABAN ta , ashe duk ƙarya take masa , ashe yaudarar sa take , ashe ganin yarinya ƙarama yake mata ita kuma tana masa kallon soko ?   Sakin hoton yayi tare da agogon suka faɗi ƙasa kan suturun ta da ya saya mata ya fara taku da nufin barin ɗakin    Lokacin da ya ji kafafun sa sun sauka akan ƴar ƙaramar wayar da take jefe a ɗakin , sunkuyawa yayi ya ɗauka ,    Ya kunna ta ,   Call logs ya shiga nan ya ci karo da number da aka rubuta HUBBY BB a jikin ta ,    Bi ya dunga yi yana ganin yadda suke ƙiran juna ita da number kusan kullum sai sun yi waya , " tun wajen wata guda da ya wuce , " ji yayi idanun sa na shirin kawo hawaye , a sarari ya furta ta yaudare ni , BATA SO NA BATA TAƁA SO NA BA ,"   Jefar da wayar yayi yana barin ɗakin cikin ran sa yana tunano irin baya-baya da take yi da shi a tun haɗuwar su , yadda take janye jiki daga mu'amala da shi , yadda baya ganin fara'ar ta , bata sakin jiki tayi magana da shi , bata ɗaukar sa da wani muhimmanci , ashe bata son shi ne , ashe tana da wanda take so suka yi soyayya mai girma da har ta kai su ga aikata zina , ashe shiyasa take son cikin jikin ta kamar ba shege bane , soyayyar uban cikin ne ta shafi ɗan , ashe son da take yiwa wannan mutumin ya wuce son da take yiwa ƴar cikin ta tare da ƴar uwar ta ?? Tunowa yayi da kalamar ta ta ƙarshe inda tace TANA SON SU SU DUKA ," ji yayi duk wani jijiyar da ta kafa so da ƙaunar ta cikin ran shi tana tsinkewa , son ta da ƙaunar ta suna mutuwa ,"   Bai san ina yake taka ƙafafun sa ba saboda yadda zuciyar sa ta shiga ruɗani , sai tsintar kan sa yayi a tsakiyar falon Baban su ,    Ɗago kan sa professor Mustapha Dilmari yayi ya dube ɗan nasa , tashin hankali da damuwar da ya hango a fuskar ɗan nasa ya sanya shi ajiye doguwar jaridar "daily trust" ɗin da ke hannun sa ," yace da shi    Doctor yaya yarinyar nan ta sauka lafiya ?     motsa bakin sa yayi maƙogoran sa na kai kawo , ya haɗa jimlar kalmar da ta tabbatu ta fito tun daga Ƙasan ruhin sa ,       TA MUTU innalillahi wa innaa ilaihi raji'oon , ta rasu ,? Wajen haihuwar ? Allahu Akbar , yi sauri ka sanar da jama'a a zo ayi mata sutura , ina abun da ta haifa ko tare suka tafi ,? "   An mata sutura a chan asibitin kamar yadda aka saba yiwa ƴan gudun hijira ƴan uwan ta idan sun rasu ba'a jiran mutanen su ,"ma'aikatan asibiti tare da sauran Al'ummar musulmai suke sallatar su a wuce da su makwancin su  ,,"    Daga haka ya miƙe ya bar mahaifin nasa yana jero addu'o'in da ake yiwa mamata ,    Bai jin yayi kuskure akan kalmar da ya furta ga mahaifin sa , ƙwarai ta MUTU  a cikin zuciyar sa kamar yadda cikin kowanne daƙika ɗaya yake sake yakice ta tare da nesanta ta da duniyar sa nisa irin na har abada , Shi yayi ƙarya ga mahifin sa da ƴan uwan sa , ya wanke ta ya rufa mata bargon asiri tare da kyautata mata zato da kyakkyawar niyyah, yanzu da kome ya bayyana gare shi ya fahimci wacece ita ,  dan haka ya sake yin wata ƙaryar da yake fatan ta zama babbar ƙarya ta ƙarshe da zai yi a rayuwar sa yayi amfani da ƙaryar ta hanyar zare ta daga rayuwar duk wani da ya shafe shi tare da shafe babin ta cikin rayuwar duk wani nasa domin ita ɗin bata chanchanta ba ... Shiru shiru Amne bata ga dawowar hamza ba da take tsumayen ganin sa tare da yakaka tayi ta ƙiran wayar sa shiru ba'a ɗauka Ga kuma baby da take ta faman tsanyara kukan yunwa duk da cewa tun shigowar su ta ɗaura ruwan zafi ta wanke jaririyar tas ta sauya mata kaya tare da diaper a cikin kayayyakin ta da suka zo da su daga asibiti , amma daga lokacin da aka haife ta tun hantsi zuwa yanzu la'asar sakaliya dole jaririyar ta ji mummunar yunwa , Gefe guda ƙarin damuwar ta na ga Falmata wacce tun tana kuka ƙasa-ƙasa , zuwa yanzu kuka take riris tana ambaton sunan yakakar babu tsahirtawa , tayi rarrashin duniyar nan Falmata taƙi shiru , taƙi ci taƙi sha , sallah ma sai da tace ta tashi tayi addu'ar Allah ya sa yakaka na a halin lafiya sannan ta tashi tayi , Ganin dare na neman yi babu abun da zata bawa ƴar jaririyar nan ya sanya ta rufe kai ta nannaɗe jaririyar da kyau ta ɗau kuɗi mai ɗan yawa ta fita nemo mata abinda zata ciyar da ita da shi ,"  kasantuwar a kusa da kasuwa unguwar tasu take , dan haka bata sha wahala ba wurin samun madarar jarirai mai kyau tare da feeding bottle a ɗaya daga cikin shagunan da suke jikin kasuwa wanɗanda basu kai ga rufewa ba ta saya , ta tsallako titi zuwa gida, Wurin da ta bar falmata nan ta tadda ta zaune kan ta haɗe da jikin bango ,    Bata bi ta kan ta ba kamar yadda falmatan ma bata nuna taji motsin ta ba , ta kwantar da jaririyar ta wanke feeding bottle ɗin ta haɗa mata madarar dai-dai yadda aka ka'idance  da ruwan ɗumi , ta ɗan bar ta ta huce dai-dai yadda jariri zai iya sha ta ɗauke ta tayi bismillah , ta fara bata ,     Nan take kuwa ta kama bakin feeder tana jaa ,    Sannu sannu sai da ta sha fiye da rabi , bacci ya ɗauke ta , Ganin ta maida kan falmata bayan ta shinfiɗe jaririyar ,"   Tausayin falmatan ya tsarga mata , cikin ɗan zaman da tayi da yaran lokacin bikin zainab ta fahimci yadda yaran suka shaƙu da juna suke kuma ƙaunar juna tare da tattalin juna ,    Ɗan ƙaramin tsaki ta jaa lokacin da take ɗaukar wayar ta domin sake ƙiran Doctor Hamza ,    Ni ban san ina ya bar wayar ba haka , ina ta ƙira baya ɗauka ya bar mu cikin fargabar halin da yarinyar nan ke ciki bari na ƙira Rahima naji ko yana gidan ne ," Bugu ɗaya Rahima ta ɗauka ta ɗauka   Abnaty ina yayan ku ne ? yaya an san inda yarinyar nan ta tafi kuwa ?   Shiru Rahima tayi tana ƙoƙarin tsayar da ƙwallar idanun ta ,"   Yayan mu ya dawo tun ɗazu hankalin sa a tashe , ya shiga sashin sa ya kulle , sai yanzu da naje gurin Baba , yake sanar da ni wai ashe yakaka ɗin ta rasu ne wajen haihuwa ,"     Innalillahi wa inna ilahi raji'oon Amne ta ƙara da salati ,    Bata ce kome ba ta sauƙe wayar daga kunnen ta , tare da kai kallon ta ga falmata wacce tayi kasaƙe tana son fahimtar  menene ,:       Muryar ta ƙasa tace Amne wai me Rahima tace ? Wani abu ya samu yakaka ko ? Amne Dan Allah kar ki ɓoye min ni da yakaka bama boyewa juna kome , yakaka ita ce kome na , ita ce mama na , baba na yaya ta kuma ƙawa ta meye ya same ta ? Dan Allah ku kaini na gan ta ,      ta furta hakan tana me sake fashewa da wani sabon kukan da yasa hawaye silmiyowa bisa ƙuncin ta , tana jin wani tsohon miƙi makamancin raunin da zuciyar Falmata ke ciki yana ɗanyencewa cikin nata ran , amsa kuwwar kalmai makamanta wannan da suka fito daga bakin Rahimar ta yana maimaituwa a kunnuwan ta ,"   Sai ta gaza rarrashin Falmatan . Washegari Bayan fitowar doctor Hamza daga masallacin sallar asubah kai tsaye sashin mahaifin sa ya shigo kamar yadda ya saba , kan shi a ƙasa suka gaisa da mahaifin sa wanda yake nazarin ɗan nasa ba tun yau ba ya fahimci akwai wata ɓoyayyar manufa a zuciyar ɗan nasa game da yarinyar ya bari ne yaga iya gudun ruwan sa , amma tundaga yadda ya ɗau komen su da muhimmanci ya fahimci yana da ra'ayi akan ɗayar su ,"   Tausayin sa ya ji mutuwar yarinya da irin birkicewar da yayi ya sashi fahimtar wataƙila ita zuciyar sa ke ra'ayi Addu'a ya sake yi masa sannan ya ɗora da tambayar sa ina ƴar uwar ta ? Nan yayi shiru ,   Kafin yace Suna gidan Amne ita da jaririyar da uwar ta bari , Nan take fuskar professor ya sauya   Gidan Amina ?    Me kuma ya kai su gidan Amina ? Na kai su ne wai dan ta kula da su musamman ma jaririyar .   Ita Amina MACE ɗin ce za'a bawa kulawa tare da tarbiyyar yara mata har biyu ? ?  To ban amince ba maza idan gari ya gama haske kaje ka zo da su , tunda ka kawo yaran nan gidan nan ikon su ya bar hannun ka ya dawo ƙarƙashi na , ni nake da ikon kulawa da su , nima ina ƙwaɗayin samun ladan rikon marayu da marasa galihu , kan Ji na ko ?    Toh Baba Ya amsa yana jin wani sabon tirniƙin ɓacin rai na taso masa sam sam baya son wani abu ya sake haɗa shi da kome ƙanƙantar abu wanda ya shafi yarinyar nan , daren jiya kwana yayi bai yi bacci ba saboda yadda ran sa yake ƙuna game da abun da yarinyar tayi masa , juyi ya dunga yi yana mamakin halin MACE , Shi a son ran sa ya bar su a chan wajen Amne ɗin lokaci lokaci yana zuwa yana kai mata abunda zasu buƙata domin a zahiri shi fatima da jaririyar ma bai son ganin su ," gani yake ita ma ƙanwar tata ta san kome tare suka haɗa baki , " shi yanzu ya bar ganin ƙanƙantar su tare da musu kallon matausaya ," ya tsinke akan lamarin MATA Ba yadda ya iya haka ya shirya kafin ya wuce aiki yaje gidan Amnen inda ya tadda ta tana yiwa baby wanka jikin ta duk a sanyaye ta kwana da zancen mutuwar yakaka sosai yarinyar ta shiga ran ta saboda yanayin kamanni sosai da take da ƙanwar ta  Rahima ,   Bai yadda ya ɗora idon sa kan jaririyar ba suka gaisa da Amne tana sake jajanta mutuwar yakaka tare da yi mata addu'a ta ɗora da tambayar sa aina aka yi jana'iza    Kaucewar tambayar yayi ta hanyar cewa ina ita ƙanwar tata ??      Tana wanka tun jiya take abu ɗaya ,"kuka ," kuma har zuwa yanzu bata kai ga sanin mutuwar ƴar uwar ta ta ba , ban ma san wanne irin hali zata iya shiga ba idan ta samu labari ," sai dai ka san hanyar da zaka bi ka kwantar mata da hankali kafin ka sanar mata da mutuwar nan  Cikin ƙagauta Hamza yace    Wane rarrashi Amne kowa ai zai mutu ki gaya mata kawai yayar ta mutu , kuma ki bata baby ta zo mu koma gida Baba ya ce na mayar su gida ...     Ƙarar faɗuwa da suka ji shi yasa Amne fitowa da gudu bayan ta shinfiɗe jaririyar , Doctor hamza ko gizau bai yi ba hasalima tun tsayuwar falmata a gun ya gan ta , yi yayi kamar bai gan ta ba , da hikimar sa na son fahimtar ko falmatan ta san kome da ya faru ? Ganin yaƙi fitowa yasa Amne kwala masa ƙira ,"      Ka fito ka ga abun da yarinyar nan take yi , kar ita ma ta mutu ," tace da shi cikin ɗaga murya Shi da kan sa ya tsorata ya kuma ji tausayin yarinyar lokacin da ya fahimci ciwon ta na asthma ne ya tashi , gaba ɗaya numfashin ta ya siƙe yana neman ɗaukewa bata cikin hayyacin ta ,    Da taimakon Allah da dabarun sa na likita , numfashin ta ya dawo ,   Zumbur ta miƙe zaune tare da kufcewa daga riƙon da Amne ta mata , lalube take tare da faɗin    Ina yaya daktan , ina kake yaya dakta , Dan Allah Dan Allah ka kai ni wajen Yakaka , naji kun ce wai Ta mutu , wai yaya ta ta mutu , ai wasa kake ko ? Yakaka tana gida ko ? Yaya za'a yi yakaka ta mutu ta bar ni ? Alhalin ta san bani da kowa sai ita , bani da ƙarfi kun gani fa ni miskiniya  ce Dan Allah kar ku min irin wannan wasan ,"    Yaya dakta ka min magana mana , tace haka lokacin da ta samu nasarar chafko rigar sa ta rike tamau ,   Yaya dakta Dan Allah   Ta sake cewa muryar ta tana wani irin harɗewa ,    Ji yayi wani mugun tausayin ta ya rufe shi yaji ina ma bai ambaci kalmar mutuwa ba , cikin ƙwarar makafin idanun ta da suks firfito suka sauya launi tamkar ba nata ba yake iya hango irin firgici tare da azabar da zuciyar ta ke ciki ,    Kukan da baby ta tsanyara shi yasa ta yunƙura da gudu tayi sashin da taji tashin muryar jaririyar , kafin su taro ta har ta faɗa ɗakin kasantuwar ɗakin da ɗan zurfi ya sa ta faɗa ciki sakamakon jefa ƙafar da tayi nan take ta gurɗe ta tafi ta faɗi , bata haƙura ba ta rarrafa da gudu sashin da take jin kukan jaririyar    dai-dai da shigowar su    da lalube ta ɗauke ta ta riƙe ta gam a cikin jikin ta , "        Idan ni bakwa tausayi na Dan Allah ku ji tausayin jaririyar nan ku kai ta wajen maman ta ni da yakaka mun yi Alƙawari zamu haife ta mu rene ta mu biyu mu bata kulawa mu biyu ,    Meyasa yanzu zaku ce Yakaka ta mutu  ? WAYE NI DA BABY IDAN BA YAKAKA ? WAYE ZAI KULA DA MU ?    ALLAH shine zai kula da ku Fatima , Amne ta ce tana sharar ƙwallar tausayin yaran , shi da kan sa hamza idanun sa sun kaɗa , tsanar yakaka na sake taso masa ,"   Wani irin kuka falmata take har tana tsuma ,"    Baba , Mama , yaana , Bulama Yakaka duk kun mutu ? Kun mutu kun bar ni ni kaɗai ?  Ni meyasa ban mutu ba nima ??    Kiyi haƙuri Fatimah kowanne me rai zai mutu lokacin sa kowa yake jira , kiyi musu addu' a    Kawo baby na shirya ta ku tafi ," Amne ta furta hakan tana mai ƙoƙarin amsar jaririyar ,   Wani irin janyewa Falmata tayi da ƙarfi ta sake ƙanƙame yarinyar ,"    Ki bar min ita kar kowa ya taɓa ta bani da kome bani da kowa sai ita , ita ma haka , ita ce jini na kaɗai a duniya ita ce ƴar uwa ta madadin dangina gaba ɗaya , ita ce HASKEN da zan iya gani da ido na , kar kowa ya taɓa ta , kar kowa ya taɓa ta , kar kowa ya taɓa ta , ta dunga maimaitawa kamar bata cikin hankalin ta ,    Da ƙyar ta yadda Amne ta sanyawa babyn diaper tare da kayan sanyi tana riƙe a hannun ta ,   Wani irin yanayi take ciki , kamar ɗaukewar ruwan sama hawayen fuskar ta suka tsaya , ta kuma haɗe labban ta wuri guda bata cewa ƙala , sai ajiyar zuciya da take akai akai , lokaci zuwa lokaci laɓɓan ta na motsawa ," A haka suka fito Amne ta kama ta ta sanyata a mota tana rungume da jaririyar da ruwan ɗumi ya ratsa ta take ta baccin ta kasantuwar tun farar safe Amne ta cika mata ciki taf da madara ,"    Motar su tana tsayuwa Rahima wacce daman tana dakon jiran zuwan su , ta fito da gudun ta tana kuka ta rungume Falmata ,     Wacce take ƙiƙam bata kuka kuma bata ce ƙala ba , "   Sashin Baba ya kai ta , ta ɗurkusa guiwar ta biyu a ƙasa tana rungume da baby ,    Muryar ta chan ciki ta gaishe shi kan ta a sunkuye ,  ta'aziyya yayi mata kafin ya ɗora mata da nasihu , " a ƙarshe ya ɗora da shaida mata cewa ",Hajja mai wurya," dattijuwar dake yi masa girki ita zata cigaba da kulawa da jaririyar har zuwa lokacin da zata yi ƙwarai , bata ce kome ba kan ta a ƙasa ,     Rahima ƙarbo jaririya ki kawo ta nayi mata huɗubha , wanne suna kike so a sa mata ?? Zare jaririyar Rahima tayi ta miƙewa baban su ,"    Ya sake maimaitawa wanne suna kike son a sa mata ,    YAKAKA ," tace da shi a taƙaice Jimm yayi yana mai maida duban sa ga hamza , "   Wannan ba suna mai asali bane ki faɗi wani sunan Fatima ," Baba yace da ita ,"     YAKAKA , ta sake maimaitawa hawaye na kwararowa daga idanun ta  ,    Shikenan za'a mata laƙabi da Yakaka, .     a take yayi wa jaririya huɗubha ya miƙawa rahima ta mayar ta hannun yakaka ,"    Suka miƙe suna barin falon ,   Abuja Nigeria Ƙarfe shidda na yamma su Yakaka suka samu isa garin Abuja ,"  gajiya da ciwon kai da ciwon ciki irin na ssbuwar haihuwa, zazzabi tare da dumuwar da take cinkushe cikin zuciyar Yakaka suka haɗu suka yi ligi-ligi da ita , , ta zama marar lafiya sosai sai numfarfashi take , bata ko iya buɗe idanun ta sosai , Unguwar "Gwarimpsamy baby tayiwa tsinke , tana shiga unguwar bata yi nisa ba tayi parking a bakin wani ɗan madai-daicin gida mai ɗauke da ƙaramar ƙofa da ɗan madaidaiciyar ƙofar shigar da mota da mota ɗaya zata iya shigewa ," fita tayi ta sanya ɗan mukulli ta buɗe ƴar ƙaramar ƙofar ta shiga ta ciki ta buɗo ƴar babbar ta dawo ta tada motar tare da sanya shigar da motar cikin gidan , bayan ta kashe motar ta zagayo gami da bude ƙofar bangaren da yakaka take ta taimaka mata ta fito , " Da kyar ta iya sanyo ƙafafun ta waje sakamakon yadda marar ta take karta mata , tana fitowa taji jiri na kwasar ta taku ɗaya ta iya yi jinin ya fara bin ƙafafun ta da gudu ,"    Wayyo Allah ciki na   Ta furta lokacin da tayi baya luu ta faɗi , da sauri samy baby ta taro ta tana ,"    Na shiga uku ke yaks meye haka ? Ni samira kar ƴar mutane ta mutu a hannuna daga zuwa ," abun arziki bai karɓi kare ba ,"   Kama ta ta sake yi ta mayar ta motar da sauri ta sake buɗe gidan ta fitar da motar ta kulle gidan gami da cilla motar a titi zuwa asibiti mafi kusa da ta sani tana tuƙi tana waiwaiyen yakaka wacce ta fara fita hayyacin ta ," Wani asibiti mai zaman kan sa ta kai ta inda tana zuwa aka karɓi yakaka ana tambayar samy baby meya same ta , nan ta shaida musu haihuwa tayi ɗazu da safe ɗan ya koma ," Nan dai suka shiga bata taimakon gaggawa bayan sun tsayar da gudun zubar jinin suka mata Allurai tare da ɗaura mata ƙarin ruwa , ba'a ɗauki lokaci ba ciwon ya lafa ta samu bacci ,," Agogon hannun ta Samy baby ta duba kafin ta jaa tsaki , har ƙarfe 7:40pm , wayar ta ta zaro daga cikin ƴar jakat hannun ta nan ta tadda miss calls ɗin samarin ta daban-daban , number da tayi wa suna da "Dude" ta bi bayan ƙiran ,"   Hello boo ya kake ? Daga chan ya amsa mata , yana tambayar ta inda ta bar wayar nan ta sanar da shi ta zo da ƙanwar ta wacce ta gaya masa ɗin , amma bata ji daɗi ba ne ,"    Kuna wanne asibiti ya tambaye ta   Nan ta sanar da shi asibitin da suke ," Ba'a ɗauki lokaci ba ya iso asibitin ,  mutum ne magidanci da ya tasamma shekaru arba'in da biyar , Babu kunya samy baby ta mannu da jikin sa tana masa ƙwarƙwasa lokacin da suka haɗu , kafin ya nemi da ta haɗa shi da Casher na asibitin , nan tayi masa jagora ,"    ba ɓata lokaci ya dire naira dubu ɗari , aka rubuta takaddar shaidar biyan kuɗin aka ba samy tare da sharaɗin idan chanjin su ya rage zuwa lokacin sallamar marar lafiyar za'a mayar musu da ƙuɗin su , idan kuma su zasu yi ciko ma sai su ƙaro , "    Basu tsaya sauraran sauran bayanan nasa ba suka yi wucewar su samy baby tana manne da jikin sa ," Ɗakin da aka kwantar da yakaka suka je ,   Har yanzu Alluran da aka mata wanda akwai na bacci a ciki basu sake ta ba , dan haka suka tadda ta tana ta baccin ta ,"        Wani kallon ƙasan ido yayi mata ,"    Yane baby na kin san fa nayi shirin daren yau tare da ke , sai kuma ga marar lafiya mun samu ,"      Karkaɗa masa ido tayi ta wani rausaya ,     Boo yadda kake so haka za'a yi , zamu iya tafiya mu bar ta ai ƙarƙashin kulawar ma'aikatan asibitin , ni da kaina nayi tanadin daren yau domin ka , ta ƙarasa zancen tana kashe masa ido ,"    Wata shashar dariya ya sake kafin ya juya yana cewa    Baby na kenan shi yasa nake daɗa jin ki a cikin jini da tsoƙa ta , bari naje mu gama da ma'aikatan asibitin game da waɗanda zasu kula da ita , sai na dawo mu wuce ,"           Samy baby tare da farkan ta , basu yi tunanin a irin halin da ƴar mutane zata iya farkawa cikin dare ba , suka yi tafiyar su sheƙe ayar su suka bar ta ƙarƙashin kulawar biyu daga cikin nurses ɗin asibitin waɗanda Alhaji Gali ya danƙa musu hatimin nasara a hannun .       Yakaka ba ita ta farka ba sai wajen ƙarfe uku na sulusin dare , ta tashi bata jin ciwon kome illah rashin ƙarfin jiki da kuma ƙirjin ta da take ji yayi nawi a sakamakon ruwan nono da ya zo ,"     Yawo tayi da idanun ta , ta tabbatar babu kowa a ɗakin sai ita kaɗai , miƙewa tayi ta zauna tare da zuro ƙafafun ta ƙasa tana bin ɗakin da take da kallo wanda yake wadace da hasken lantarki ,     Hotunan abubuwan da suka wakana tun daga safiyar jiya su suka yi ta dawo mata ɗaya bayan ɗaya , kamar a lokacin suke faruwa ,"    Wani irin kuka ta fashe da shi lokacin da tunanin ta ya kawo ta dai-dai wurin da take sanya ƙafafu tana wucewa ta gaban falmata ba tare da ta tsaya ta mata magana ba barw tayi mata sallama,damuwar da ta hango a idanun falmata a lokacin da ta waiwaye ta da kallon ƙarshe a jiya , ta tabbatar damuwar da take kwance idanun falmatan ya assasa ne ta dalilin rashin sanin halin da take ciki , ji tayi zuciyar ta ta kumburo da ta lalubi son sanin halin da falmatan take ciki har ta kwatanta a yanzu ,    Wayyo Falmata na ta furta a sarari tana dafe ƙirjin ta , yunƙurawa tayi ta tashi da sauri ta nufi ƙofar ɗakin , kamar wacce aka dakatar kuma sai ta tsaya , tsayuwar ta baya rasa nasaba da tunowa da tayi a bigiren da take a yanzu wanda yake da tazara mai tarin yawa tsakanin ta da inda ta baro Falmata ,"    Ruwa mau ɗumi ta ji yana kwarara ta cikin rigar ta da ya sata saurin janye rigar ta ga menene ??     Ruwan nono ne yake zuba ," tuno da ɗiyar ta da ta bari ba tare da ta kai ga ko ganin fuskar ta ba tayi , kukan da ta baro ta tana yi wanda ta tabbatar na yunwa ne sautin sa take iya jiyowa tamkar a yanzu take ji , wani irin tausayi ne tare da wani iri lamari mai girma da ya zarce nadama taji yana bin jijiyoyin jikin ta da gudu kafin ya zo ya watsu cikin zuciyar ta , "     Zubewa tayi akan guiwowin ta ta baje a ƙasa tana sake sakin wani ƙaƙƙarfan kukan da yake ɓullowa tun daga ƙarƙashin ran ta ," Ƙarfe shida na safe nurses ɗin da aka bawa ajiyar yakaka suka shigo ɗakin da take su biyu , ɗayar riƙe da magunguna tare da allurai .,"   Turus suka yi lokacin da suka ga gadon da take babu kowa , a tsorace suka ƙarasa shigowa ɗakin ,"   i Ina take suka haɗa baki wajen tambayar junan su ??    Kamar ance su waiga suka hango ta zaune a ƙasa daga jikin bango ta takure ƙafafun ta ɗora hannayen ta bisa guiwowin ta gami da kwantar da kan ta akan hannuwan ,"   Kin tashi ne ?  A ah ya kika zauna anan ?    Ɗayar nurse ɗin ta tambayi Yakaka suna matsowa kusa da ita ,    Ko gizau bata yi ba Duk da cewa idanun ta a buɗe suke ta kafe su a jikin bango ,"    Kallon juna nurses ɗin suka yi ," Patient da ke muke fa , ko bakya jin hausa ne ?      Motsa bakin ta tayi ƙasa ƙasa tace Ina anty samy ?     baki da lafiya ne ? Kizo ki hau gado mu auna ki kisha maganin ki na miki allura kafin doctor naki yazo , yayar ki bata kwana a nan ba sun fita da mijin ta sun ce zasu dawo da safe ,"    Wasa gaske , ƙememe Yakaka taƙi miƙewa daga gurin da take takure a zaune , a ƙarshe dole suka haƙura suka bar ta a wajen suka yi tafiyar su shirye shiryen tafiya gida saboda masu aikin safe zasu karɓe su , suka rubuta a cikin folder nata taƙi yadda ta sha magani kuma taƙi yadda ayi mata allura ,"   Tara na safe ta gota aka turo ƙofar ɗakin aka shigo , samy baby ce ta shirye tsaf cikin wani ɗanɗasheshen yadi , hannun ta riƙe da ɗan kwando wanda ta zubowa yakaka abun ƙarin kumollo ,    Ita ma sai da zuciyar ta tayi tsalle da ba ta hango yakaka saman gadon asibitin ba ,          Chan gefe ta hango ta , da sassarfa ta nufi wajen ta tana     Yaks ya kike zaune a ƙasa lafiya dai ko ?      Tana jin muryar samy baby ta miƙe tsaye gami da takowa da gudu ta riƙe hannun samy baby ta shiga roƙon ta ,"       Anty samy Dan Allah kiyi sauri ki kaini wajen sa , ya mayar da ni gida na koma wajen su Falmata , ji nake kamar zan mutu ,       Da ido samy baby ta bita tana iya hango tashin hankali tare da ruɗani gami da tsantsar rikici a idanun Yakaka ,"      Ke yaks bana son shirme ki nutsu , haka kike so na ɗauke ki yarkace-yarkace daga gadon asibitin na kai masa ke ??     Ai wannan sai ya kore ki Bazai kore ni ba anty samy shi zai kai ni a min gyaran jiki ,"    Mtss samy baby ta jaa tsaki , Ki zo kici abinci Yakaka tun jiya rabon ki da abinci , nurse ɗin sun baki magani tare da allura ? Ki ci abinci ki gyara jikin ki kafin likitan ya zo ,"   Warce hannun ta da samy baby ta riƙe tayi , ta durƙusa gami da haɗa hannun ta ta shiga yi mata magiya tana gunjin kuka akan lalle fa ita a yanzu zata kai ta wajen bature kam silum kuma a yau zata koma wajen su Falmata ,"     Tun samy baby na ƙoƙarin rarrashin ta tare da yi mata dabara har ta suƙe ta fara yi mata masifa ,     Faɗan da ta fara yi mata bai haifar da kome ba sai sake rikicewar Yakaka domin kuwa yunƙurawa tayi da gudu tana ihu ta nufi ƙofar ficewa daga ɗakin da nufin komawa gida ,"   Da gudu samy baby ta ruƙo ta kafin ta kai ga ficewa daga ɗaƙin , hankalin ya fara tashi ita ma , sam bata yi zaton yakakar zata birkice mata irin haka ba , " sai tayi da gaske tare da taka tsantsan idan ba haka ba zata jawo mata jangwam kowa ya san haƙiƙanin abun da ya faru daga ƙarshe ita ce zata iya faɗawa hannun hukuma ayi ram da ita ,"       Ke yaks Ke yaks ƴar iska meye hakan kike min ? Ina cewa da yardar ki da amincewar ki muka taho ? To shikenan gyara jikin ki ki sauya kayan ki da wannan rigar ta miƙa mata wata doguwar riga a cikin leda tare da audugar mata da sabbin panties , shirya mu tafi ,"     Ba musu yakaka ta karɓi rigar tana jan ajiyar zuciya irin na wanda ya ci kuka sosai , ta shiga banɗakin wajen ta gyaro jikin ta gami da sauyo kayan ta ,"    Kwandon abincin samy baby ta ɗauka suka fito daga asibitin ba tare da sun yiwa kowa sallama ba bare su bi ta kan chanjin su da samy baby ta tabbatar akwai ,"    Gidan da yake mallakin ta ne wanda ta fara kai yakaka jiya nan ta sake yada zango ,inda tayi wa yakaka umarni da ta fito ba musu ta fito , ta taka ta bi bayan ta zuwa cikin gidan inda ta sa ɗan mukulli ta buɗe wata ƴar kwatatciyar ƙofar madaidaicin falon suka shiga kai tsaye samy baby ta wuce jikin wata ƙofa da take daga gefen hagu a cikin falon ta sanya ɗan makulli ta buɗe kofar ta sanya kai ciki ,      Yakaka tana dogare daga bakin ƙofar falon ta ji muryar samy baby na ƙiran ta daga cikin ɗakin da ta shiga ,   cikin ɗakin ta shiga gami da durƙusawa daga baki-baki tace   Na'am Anty samy   Tashi ki ƙaraso yakaka nan ɗakin ki ne , na shirya miki shi tun kafin na kawo ki , ga banɗaki nan shiga kiyi wanka na haɗa miki ruwa mai zafi sosai da zaki gasa jikin ki , idan kin fito ga gado ki kwanta kiyi bacci idan ya so in kin farka kin cin abinci kin nutsu sai muyi magana ,"   Tunda ta fara magana Yakaka ta ɗago idanun ta tana kallon ta ,gama maganar ta ya zo daidai da silalowar ƙwalla daga idanun Yakaka , da kyar ta harhaɗo kalmomin da zata iya amfani da su    Anty samy cewa kika yi shi yace ki kaini wajen sa , na ɗauka tun jiya zaki kai ni ? Dan Allah ki kai ni bazan zauna anan gidan ba ,"   Kallon baki da hankali samy baby ta watsa mata , ai kuma sai kiyi tunda ke kunnen ƙashi ne da ke bakya jin maganar mutane , tace tana kewaye ta ta fice daga ɗakin har ga Allah ta fara ganin gangancin kan ta da ta ɗauko yarinyar nan ta zo da ita nan ba tare da ta mata bayanin haƙiƙanin gaskiyar manufar ta ba , kar fa ta zame mata matsala !     Zama tayi akan ɗaya daga cikin ƴan kananun mannanun kujerun da suka zagaye falon suka yi ɗas gwanin sha'awa ,        Ta ɗauki wayar ta da nufin ƙiran ƙawar ta ,"    Yakaka ta gani ta fito ta tsaya akan ta jikin ta sanye da dogon hijabin da ta bata jiya ,"       Ɗurkusawa tayi a gaban ta cikin wata irin murya chan ciki tace     KI MAIDA NI GIDA ANTY SAMY ," Da sauri samy baby ta miƙe tsaye    Ke Yakaka kar ki min iskancin banza da rashin kunya ,     To bari ki ji na faɗa miki Gaskiya ni taimakon ki nayi na tsamo ki daga cikin hallakar da wannan Doctor yake neman jefa ki ta hanyar ƙulla soyayya a tsakanin ku , alhalin ya san cewa sofi na nan na dakon soyayyar sa shekara da shekaru , ni nasan irin Alkaba'in sofi da Alwashin da take ci akan duk wata mace da ta raɓi Doctor Hamza , da bana fatan ko kusa ki faɗa cikin kaidi tare da masifar ta , shi yasa na zare ki daga cikin rayuwar doctor baki ɗaya na kawo ki nan waje na domin na inganta miki rayuwa na tsaya miki ta yadd watarana za ki zama macen da ire iren Sofi da waɗanda suka fi ta zama annoba ma basu isa ɗaga miki ɗan yatsa ba , amma dayake ke ƴar iska ce WAWIYA JAHILA ,kina neman butulce min akan wani sakaren makahon son abunda baza ki taɓa samu ba da kike yi ,    ki buɗe kunnen ki kiji da kyau ni ban san inda wani yarima yake ko wa ? Ban san inda yake ba abokin sa nuhu da kan sa bama tare , dan haka dabara kawai nayi miki tare da aiki da ILMI NA , dayake ke wawiya ce kika yadda kika amince wani ɗan sarki wai yana ƙiran ki , Ɗan sarkin da kuka yi tarayyar kwanaki kaɗan domin samun muradin zuciyar sa kaɗai , ɗan sarkin da ya miki ciki ya jefar ki kan titi ya yi tafiyar sa ya bar ki ba tare da ya sake waiwayar ki ba , ɗan sarkin da dake da babu duk ɗaya ne a wajen sa , ya ma jima da mantawa kin taɓa wanzuwa a rayuwar sa , wanda yayi watsi dake tsawon wannan lokacin amma shine kika yadda wai yana ƙiran ki wai yana ƙiran ki a hakan nan naki ,!     Ta ƙarashe tana nuna ta da ɗan yatsa kafin ta kwashe da dariyar walaƙanci ,"      Kin san meye yaks , idan zaki tafi Ban hana ki ba ga hanya ki fita amma ki sani nan Babban birnin tarayya kike Abuja , cike take da mutane mabanbanta wanda masifar da take tare da wasun su ta kai girman da ya zarta tunanin ki , abune mai sauƙi a sace ki a ɓatar da ke ɓata na har abada ,"    Zaɓi ya rage gare ki ki zauna tare da ni ki gina kan ki ta yadda watarana zaki koma ki ɗauko ƴar ki tare da ƙanwar ki ki musu rumfa ki zama gatan su , ko kuma ki fita da nufin komawa masu amfani da mutane wurin yin tsafi suyi gaba da ke su hallakar ki , Wataƙila ki samu nasarar komawa garin maiduguri kije ki auri doctor Hamza,  sofi ta taso bisa kan ki a ƙarshen ƙarshe ki hallaka a hannun ta , masifar sofi bazai tsaya iyakacin kan ki ba , har makauniyar ƙanwar ki tare da ƴar da kika haifa sofi sai ta ɗau fansar raɓar mata doctor da kika yi ,"    taku ta fara yi tana barin falon bakin ta na sake furto kalmar ,shawara ta rage gare ki BANZA WAWIYA JAHILA , Kalma-bayan-kalma kalaman samy baby ke yin dawurwura cikin kunnuwa suna zarcewa ga kwakwalar yakaka , sai dai fassarar su sun gagari ƙarfin tunanin yakaka ,    Meye tace ne ? Me take nufi wai ? Anty samy tace ni wawiya ce jahila amma ai bata ce ni mahaukaciya bace , alhalin kuma ni nasan na haukace ne ,"    Zamewa tayi ta kwanta a tsakanin kujerun gurin tare da curewa ta duƙunkune cikin hijabin jikin ta , fata take a mata wani mummunan mari , ina ma fankar da take juyawa a sama zata faɗo ta daki kanta ko zata samu ta farka daga mummunan mafarkin ido biyun da take ,"     Wai Anty samy duk daman ƙarya take mata , wai Anty samy yaudarar ta tayi , wai daman ashe Bature kam silum ya jefar ta ne ba tare da ya taɓa neman ta ba , ashe ya manta da ita , ita ke dakon soyayyar sa , wai ashe ashe an raba ta ne da Doctor hamza mai taimkon su ita da ƙanwar ta , tuno da shi tayi da tashin hankali tare da tausayin da ta hango ɓaro-ɓaro cikin ƙwayar idon sa lokacin da take cikin magagin ciwon naƙuda , ajiyar zuciya ta fara saki da sauri da sauri tana jin yadda tsokar jikin ta take ƙarƙarwa sakamakon wani mugun sanyi da taji yana lulluɓar ta ,"     ME NAYI WA ANTY SAMY DA TA JEFA RAYUWA TA A WANNAN MASIFAR ?? Tambayar da ke yawo cikin zuciyar ta kenan lokacin da take rufe fatar idanun ta da ko ɗiris babu ɗigon ƙwalla , "wani tashin hankali yafi gaban kuka ,"       Sai yamma liƙis samy baby ts fito ta sha wankan ta ta haɗe cikin wata diguwar rigar roba mai bin jiki , kasantuwar ta ƴar chas-chas sai tayi kyau a cikin kayan ," bata ga yakaka a falo ba dan haka sai ta leƙa ɗakin da ta mallaka mata nan ma har cikin banɗaki ta leƙa babu alamun ta shiga cikin sa dan haka ta fito da sauri da nufin leƙa waje ko dai ta fita ɗin ne da gaske ???      Cin karo tayi da ita kwance a inda ta bar ta tun safe , ta Ƙudundune daga kan ta har ƙafafun ta , wani irin tausayin yarinyar ta ji ya taso mata , ita da kan ta ɗazu ta jima bata yi bacci ba da ta kwanta tana ta saƙawa da warwarewa , ganin laifin kan ta take , akan ƙaryar da tayi mata ta zo da ita ba tare da Aminccewar ta ba yayin da wani sashi marar  ƙarfi kuMa ke ganin ai daidai tayi taimako tayi kamata yayi ta Gode mata , Sunkuyawa tayi tana tashin ta a hankali ,"    Yakaka , wacce daman ba bacci take ba ta janye hijabin ta ɗago kan ta tana fatan ta buɗe ido ta ga kome mafarki ne , ta gan ta a ɗakin su da Doctor hamza ya mallaka musu , tare da ƙanwar ta , baby mama kuma tana fatan taji motsin ta a cikin cikin ta ,   Ganin samy baby ce ke tashin ta cikin gidan da ta tabbatar nan ƙaddara ta jeho ta rayuwa cikin sa , yasa ta ji zuciyar ta na yadda da abunda tunanin ta ke tabbatar mata cewa ba mafarki bane , kome ya faru ne a zahiri , ita yakaka a duniyar da take yanzu ita kaɗai ce jal , babu Falmata babu abunda ke cikin ta babu kuma Doctor Hamza mai taimakon su , duk tayi musu bara'a ta tsallake su bisa jagorar wawancin ta tare da jahilci da suka biyo ta kan mummunar rufa-rufa tare da gadar zaren da samy baby tayi mata , da taimakon ta ta aikata babban kuskuren da baza ta taɓa yafewa kan ta ba ,"    Kallon samy baby take kamar yadda ita ma samy baby ke bin ta da kallon tausayi ,    yakaka ki tashi haka Dan Allah ki je ki ci abinci kiyi wanka ki gasa jikin ki , kin san fa jego kike ina miki tsoron kar jikin ki ya lalace ,    Toh tace tana mai yunƙurawa ta mike , da sauri  samy baby ta kama ta kai tsaye banɗaki ta kai ta tare da sake haɗa mata ruwa mai zafi tace tayi wannan sosai ,"   Toh     ta sake amsa mata ," cikin daɗin ran fara samun haɗin kan yakaka samy baby ta nufi ɗan kitchen ɗin da taje da shi a gidan domin dafawa yakaka ɗan wani abu mai sauƙin dahuwa da zata iya ci ,    Nan da nan ta dafa mata indomie ruwa-ruwa da soyayyen ƙwai guda biyar ta haɗo da ruwa ta kai mata ɗakin , nan ta tarar da ita zaune akan tiles ɗin ɗakin ta har lau tayi wanka ta maida kayan jikin ta da hijabin da ta cire     Yakaka kul ki daina zama haka a ƙasa jego kike ba'a son mai jego tana zaman ƙasa tashi ki koma bakin gadon ga abinci ki ci , zan kawo miki wani kaya ki sauya kafin ki warware muje ayi miki sabbin ɗinki kin ji ?   Toh Tace tana miƙewa ta zauna a bakin gadon kamar yadda tace .    Wasa-wasa cikin sati guda da samy baby tayi tana gida kullum tana kula da yakakar , ta lura tamkar yarinyar ta koma shiru-shiru , wacce ta samu taɓin hankali bata un bata un'un kome tace mata kawai "toh" take cewa    Hirar duniya wacce take bukatar bada amsa samy baby tayi wa yakaka amma yakaka taƙi cewa uffan , iyakaci idan ta bata umarnin yin abu take zata yi babu gardama,    Ranar da ta cika sati da kawo ta gidan ta shiga ɗakin yakakar da safe , cikin ran ta tana aiyana idan har ta tabbatar yarinyar nan ta samu matsalar taɓin hankali ne , sauri zata yi tasan yadda tayi ta maida ta inda ta ɗauko ta , ah to ita ina zata iya rainon mahaukaciya ?     Zaune ta tadda yakakar tayi jigum tana kallon windown ɗakin ,"    yaks ya kike jin jikin ki yau ? samy beby ta tambaye ta ba dan tana sanya ran samun amsar yakaka ba , ga mamakin ta sai ta ga yakakar ta juyo da kallon ta kan ta , cikin wata muryar dake fitowa da sauti marar amo tace     ANTY SAMY KI KAINI MAKARANTA , KI SAKA NI A MAKARANTA INA SO NAYI KARATU INA SO NA SAMU ILMI. Wata irin dariyar murna samy baby tayi tana mai zama gefen gadon ta riƙo hannayen yakaka ,    Yaks , yaks ko kefa ? Kin fara fahimta ta ko yaks ? A yau yau zan sanya a fara nemar miki makarantar da za'a sanya ki , nayi alƙawarin karatu sai kin gaji yaks , Ilmi ai shine gishirin rayuwa bari ki ga ina wayata ?  Bari naje na ƙira Alhaji Gali , makaranta sai wacce kika zaɓa yaks , tace tana ƙarasa barin ɗakin har da ɗan gudun ta , Da ido yakaka ta bita cikin ran ta tana sake ɗaura ɗamarar goge kalmar JAHILCI daga gare ta da tafi bada tabbacin kome da ta aikatawa kan ta da wanda wasu mutane suka wanzu suna aikata mata , ya faru ne ta dalilin Jahilcin ta , Kalmar wauta kuwa a cikin satin ta fara nesanta kan ta da ita , domin a ɗamarar ƴakin da ta ɗaura bata da buƙatar tafiyar tare da wannan kalmar ta wawanci da aka danganta ta da ita , " Bata sani ba ko zata iya , ko burin ta zai kai ga cika , ko watarana zata cimma manufar da ta lulluɓe cikin ranta a tsawon sati guda da ta wanzu babu dare ba rana tana saƙawa tare da kuncewa cikin ran ta , tana matse zuciyar ta tana ƙwanƙwasar ƙwaƙwalwar ta har ta samawa kan ta mafitar da take ganin zata iya kaiwa gaci ta hanyar ta , bata sani ba shawarar zata kai ta inda take so ko kuwa zata ɗora ta ne kan wani kuskuren , bata sani ba ta raba kan ta ne da kalmar wawanci ko kuwa ta sake tafiya ne bisa jagorancin wani wawancin ? Ko ma meye ta bar kome ta janye hankalin ta daga kan kowa da kome ta ɗaura ɗamarar yin YAƘI DA JAHILCI ."   Maraɗi Niger Tafeeda ne zaune a gaban hajiya umma ya tanƙwashe ƙafafun sa babu kowa a falon ta na ciki daga shi sai ita ,      Ka tafi zouwa nigeria ka zo min da bayani mai gamsarwa a game da abokin ka. Tabbas yana cikin wani yanayi wanda yake boyewa daga gare mu , kayi gaggawar taryar sa a chan a magance matsalar tun kafin ya samu isowa da ita zouwa cikin gidan nan , kasan dai duk wata matsalar da ta shafi yarima idan har ta shigo gidan nan ta shafi mutanen cikin masarauta ne baki ɗaya ,"  Toh ranki ya dade cikin yardar ubangiji a gobe zan fara neman iznin tafiya daga shugaba na wurin aiki , zouwa ƙarshen sati na kan iya samun iznin tafiya , ki kwantar da hankalin ki , babu abunda zai faru ga Biyamuradin maraɗi Allahu shi sa haka , haka muke fata , Allah shi muku Albarka baki ɗaya ya kare ku daga faɗawa tarkon Maƙiya , kana iya komawa yaro na ," Ameen Ameen yake amsawa , ya miƙe kan sa a sunkuye yana faɗin ki tashi lafiya ranki shi daɗe ," shiru hajiya umma tayi tana nisawa cikin tunanin meke faruwa ga yarima youssouf haka mai girma da yasa take jin damuwa har a cikin amon muryar sa , ?? Jikin ta yana bata wani abu ya faru ko yana shirin faruwa gare ta ita kan ta kyakkyawa ko kuma akasin sa , koma menene tasan yana da alaƙa da youssouf ɗin ta domin akan sa kaɗai wannan soyayya mai girma take bayyana tasirin ta a kaf cikin ƴaƴan ta !      Cikin satin kamar yadda tafeeda yace ya gama shirinsa tsaf , yayiwa nigeria tsinke , Bai wani sha wahala ba yayi wa kan sa jagora zuwa garin maiduguri bayan da jirgi ya sauke shi a garin abuja , " sai da ya samarwa kan sa masauki international hotel ya huta , washegari ya bada kuɗi aka sayo masa layin nigeria ya cire layukan sa na niger ya sanya ns Nigeria , hajiya umma ya fara ƙira ya sanar mata da samuwar sabon layin nasa da zasu dunga magana ta hanyar sa sannan , ya kashe ya fara laluben number biyamuradi youssouf wanda bai kai ga sanin isowar Tafeeda nigeria ba rabon da suyi waya ma sun tasamma kwanaki goma abun da kusan hakan bai taɓa faruwa ba a tsakanin su sai fa yanzu da biyamuradin yake cikin wani hali na tsantsar damuwa tare da ƙarin zafafawa kan sa aiki da yayi ta hanyar rashin hutu ba dare ba rana yana zabarin rundunar dake ƙarƙashin sa suna matsa ƙaimi wurin farautar ƴan tawayen Boko haram ," duk a ƙoƙarin sa na son yakice tunanin damuwar sa daga cikin ran sa da kuma kusantowar lokacin da aka ɗibar ma su na kammala aikin su da nigeria yana gaf da ƙarewa tsakanin kwanaki arba'in masu zuwa nan gaba zasu cika shekara da aka ɗibar musu za kuma su koma ƙasar su ta haihuwa ,"......! Assalamu Alaykum kowa da kowa ! ina miƙa sakon gaisuwa ta ga masu karatu ,tare da fatan Alheri ! ku sani naji daɗi na kuma yaba muku a kan yadda kuka bayyana ra'ayoyin ku kan shafin da ya gabata ," ƙwarai ƙwarai na gode muku ," Zan kuma yi ƙoƙari ganin nayi amfani da wasu daga cikin shawarwarin ku/ƙorafin da kuka yi , da fatan nima zaku bani dama ku cigaba da bibiya ta ba tare da kun yi saurin yanke hukunci ba har ku ga inda na cimma matsaya da kuma manufa ta da inda labarin ya dosa , Da fatan zaku samu wasu ƴan dakiƙai daga cikin lokutan ku kuyi addu'a ga ƴan gudun hijira da igiyar rayuwa ta chukurkuɗe musu take kuma jaan su tana haɗa su da manyan ƙaddarori duk a sanadin rabo su da bigiren su mahaifar , su garuruwan su da annabor boko haram tayi , suka tsinci kawunan su a cikin matsananciyar rayuwar da ta zarce ta su yakaka da falmata a tasku tare da wahalarwa , Annobar boko haram gaskiya ne kamar yadda wani sashi na daga cikin labarin nan yake gaskiya ! Ina matan da suke makancewa cikin so , ?  tare da sarkarwa soyayya ragamar rayuwar su , har ta kai su ga aikata mummunan kuskuren da zasu wanzu suna danasani tare da nadama cikin rayuwa , Yakaka tace ahir kuma kul ! Ba kome da kake so kake samu ba ba kuma kowanne abunda kake so bane yake zama Alheri , Rayuwar da duk aka ɗaukaka soyayyar fiye da kome a cikin ta ba'a cika yin ƙarƙo tare da samun farin cikin rayuwa ba ,! Hannun ka mai sanda ne kuma Nasiha ce !    Nagode !   Af na manta    Yakaka tace I Love y'all ta gutsuro muku kaɗan daga cikin irin son da take yiwa bature kam silum, " Ah to meye So ne fa ??? 😂    [7/9, 4:42 PM] +234 803 559 8589: Fikra writers association . MAFARI ( Hargitsin Rayuwa ) umm'muaz 28 Biyamuradi youssouf bai samu damar shigowa cikin garin maiduguri ba sai da Tafeedah ya samu kwanaki biyu a cikin garin yana dakon jiran sa ,"saboda yanayin aikin sa ," Kai tsaye hotel ɗin da tafeeda yayi masauƙi ya nufa , kasantuwa tsawon watannin da ya samu yana ɗan shigowa garin ya fara gane hanyar guraren da kafafun sa ke yawan zuwa ," Bayan sun gaisa cikin raha sosai irin ta aminan junan da suka shaƙu da juna , Tafeeda ya nisa yana kallon Youssouf ɗin tare da nazartar sa , ƙwarai ya fahimci har yanzu bai shirya sanar da shi damuwar sa ba , duba da yadda yayi ƙoƙari ya boye damuwar ta sa fiye da wancen haɗuwar tasu , cikin rashin sanin damuwar ɓaro-ɓaro ta bayyana kan ta a cikin ƙwarar idanun sa ," Kai tsaye Tafeeda ya doshi Youssouf da maganar da ta taso shi takanas daga ƙasar su ƙarƙashin umarnin hajiya umma , inda yake cewa   Ban san ba ko rabuwar mu ta ƴan watanni ta sauya alaƙar mu da kai ba ɗan ouwa , ta yadda har ta kai ka shiga boye min wani babban lamari da ya shafi rayuwar ka wanda ya kai ga tsunduma ka cikin damuwar da hatta Hajiya umma ta shina , ita ma kuma damuwar ta shafe ta ta kuma sanya ta a firgici , ka riga ka san kome na daga yanayin gidan da munka taso cikin sa , ka san kou kai wanene , kasan yadda hajiya umma ke takatsantsan da du wani lamari naka , hakan ya sa hajiya umma ta titsiye ni tana son san sani game da abunda yake faruwa gare ka , na shaida mata ko ɗaya bani da sani game da halin da kake ciki nan , sai  tayi gaugawar turo ni domun naji shin menene damuwar ka Yarima Youssouf ? Shiru ne ya ɗauki ɗakin , A haƙiƙanin gaskiya Youssouf yana kunyar buɗe baki ya sanar da wani mahaluki laifin da ya aikata tsakanin sa da ubangijin sa , laifi mai girma kuma irin wannan , to amma hajiya umma ita wata halitta ce mai girma gare shi bazai so ba ko kusa shi ya zamto silar samar da damuwa ga ruhin ta , abun zai masa yawa ," To amma wanne hali zata shiga idan ta ji dalilin shiga damuwar sa ? Wane alfanu sanar da ita damuwar sa zai samar ?  Idan ta ji laifin da ya aikata da har ta kai shi ga shiga halin da yake ciki ƙara mata damuwa zai yi daɗi da ciwon zuci ko kuwa ma hawan jini ," ! Kai anya ma kuwa zata yafe masa ?? Tunanin halin da zata iya shiga ciki kawai ya sanya gumi tsatsafo masa a goshi , hannun sa ya kai ya rufe fuskar sa da tafukan sa , ya goge gumin , Ɗan ouwa , nayi kuskure mai girma cikin rayuwa wanda giya ta zam sanadi , na haiƙewa ƴar mutane , nayi tarayya da ita har ta samu juna biyu , a yanzu haka mariƙiyar yarinyar ta kore ta ta shiga duniya . ɗan ouwa ka faɗa min ya zan yi ina zan tahi na same ta ? Yaya zan yi na gyara kuskuren da na aikata , ɗiyar mutane zata zama kilaki sanadi na , yaya rayuwar ni nawa ɗiya mata zasu ƙarƙe ?? Yaya nawa ƙanne zasu samu kariya , tayaya zan katange iyalina ? .... Kallon sa kawai Tafeeda yake idanun sa sun kaɗa jazir da ɗai bai taɓa jin zance mai munin wannan ba , ashe yarima bayan shan barasa har fyaɗe yake yiwa mata ? Har zina yake yi ?  Har ɗa ya samar ta hanyar haram ? Anya anya Yarima Youssouf ya chanchanta ?? Miƙewa yayi ya soma haɗa kayan sa ," baya so ya cigaba da kallon sa , ganin sa a halin yanzu zai ɗarsa masa tsanar sa , zai rushe amincin da suka faro tun ƙuruciyar su ," yana so ya tafi , yana so yaje ya lallashi hajiya umma da tausasan kalamai domin ita ɗin a yanzu abar a tausayawa ce , da ɗai bazai yadda kunnuwan ta su ji waɗannan munanan laifukan da ɗan da ta ƙwallafawa rai ya aikata ba , ɗan da hatta shi da kan sa yaci albarkacin samun tsaftatatciyar tarbiya daga gareta sanadin raɓar Youssouf da yayi amma sai ga shi , !  Kai kaicho Da sauri Youssouf ɗin ya miƙe yana riƙe hannun Tafeeda da yake harhaɗa ƴan abubuwan buƙatun sa cikin jaka , Warce hannun sa yayi da wani irin zafin nama     Kar ka taɓa ni Youssouf , babu wata sauran Alaƙa a tsakanin mu , manzon Allah yace mu guji munanan abokai, mu mu'amalanci mutanen kirki ," kai baka chanchanta ba Youssouf      Ƙwallar da ya kamata ta zubo tun watanni da suka gabata amma rashin samun damar kukan ya hana ta zubowa tare da taurin rai irin na soja gami da jin kai na jinin sarauta ita ce yau ta silalo ,      A hankali ya zauna a bakin gadon , bai yi aune ba ya fara kuka shaɓe-shaɓe da hawaye kukan nadama kukan tsanar kai kukan neman mafita ,"   Share shi Tafeeda yayi tare da cigaba da haɗa kayan sa tsaf ya ɗaura agogon sa gami da ɗaukar ƴar jakar sa na matafiya,      Kallon Youssouf ɗin yayi , Zuciyar sa ta raunana , ganin hawayen sa abune da tun zamanin ƙuruciya rabon sa da gani , kai zai iya ƙirga yaushe da yaushe ya ga kukan Yarima Youssouf tun a ƙuruciyar su , to ɗan sarki ne , ɗan gata yarima , da kowa tattalin sa yake ,  a yau ya san cewa zuciyar sa ta luguiguita matuƙa da har ya kawo zubar hawayen sa a karon farko cikin shekarun girman su ,     Ƙauna ta haƙiƙa irin ta shaƙiƙan aminai ta taso , ji yayi bazai iya tafiya ya bar shi ba ya zama dole ya tsaya su samar da mafita , kamar yadda suka saba tallafar junan su idan wata maysala ta riski ɗayan su kome girman ta ko ƙanƙanta,    Ina yarinyar take ?wanne hali take ciki ? Ina cikin jikin ta ? Gaba ɗaya martabar gidan sarautar maraɗi na cikin barazana , ! Dawowa yayi ya zauna a gefen sa gami da kautar da kai ,"      Sai ka faɗi wanne yunƙuri kayi wajen neman gafarar ubangiji gami da nemo yarinyar tare da wanke kan ka , ka fa sani Yarima Youssouf ɓacin sunan ka daidai yake da zubewar martaba da ƙimar mahaifin ka "Maimartaba," tare da gaba ɗayan masarautar mu ,"   A yau Yarima shi ya koma tamkar bawa da ake ba umarni babu ja ya shiga bawa Tafeedah labari tun daga ranar da kome ya fara wanzuwa a tsakanin su irin mawuyacin halin da ya shiga akan ɗiya mace a lokacin da yadda kome ya cigaba da gudana har zuwa ranar da ya tafi ya bar ta ," Tsumu Tafeeda yayi yadda yake zaton kome ba haka ya ji ba , tabbas ya san Youssouf bai yin ƙarya da garaje , yayi zaton da son ran sa ya aikata kome , amma a yanzu da ya saurati bayanin bakin sa idan kuwa gaskiya ne tabbas akwai lauje cikin naɗi ,"   Ya zama dole a nemo yarinyar nan tare da cikin jikin ta ," domin mu samu tabbacin abun da ke cikin ta bashi alaƙa da kai , domin kai ma baka tabbatar ba , bani fatan ya zam naka ne ,"   ya kuma zama dole ka gyara kuskuren ka ɗan ouwa kamar yadda kayi niyya nima ina goyon baya ɗari bisa ɗari ka taimaki rayuwar yarinyar nan son samu ...ka aurar ta ga wani !   Basu gushe ba suna tsara yadda lamura zasu musu sauƙi wajen samun ta har dare ya shiga , nan suka bar duk wani shirin su zuwa gobe ,"       ****    9pm Doctor Hamza ya kammala duk wani shirin sa da ya ɗau tsawon kwanaki goma yana yi kafin rubuta hutun ƙarshen shekara da yayi na tsawon sati shidda da zai fara daga gobe , Kamar yadda ya tsara a goben zai bar garin zuwa zaria inda yake so ya ƙare hutun nasa a chan Jami'ar Ahmadu Bello , sashin horas da likitoci inda ya ƙirkirawa kan sa wani guntun shiri na faɗaɗa ilmin sa da bincike akan sashin da yake da ƙwarewa ta fannin sa na tsawon sati shiddan , duk a ƙoƙarin sa na son ganin ya yakice duk wata damuwa da Yakaka ta ɗarsa masa cikin ran sa domin kuwa bai san yana son ta har haka ba , bai san son da yake mata yayi masa mugun kamu , ya kafu yayi rassa a cikin ran sa ba , sai cikin kwanakin da suka biyo bayan gudun da tayi ta bar shi , ya kuma gano duk wata rufa-rufa tare da yaudarar da tayi masa , kullum da tunanin abun yake rayuwa cikin ran sa , ko kaɗan bai jin sa dai-dai kewa tare da tsantsar tsanar ta da ya cusawa kan sa na barazana ga walwalar sa , aikin sa da kan sa ya fara samun tsiko a cikin sa , bai tare da kwanciyar hankalin da ake buƙatar irin sa cikin aikin sa , hakan ya sa ya rubuta Annual leave na dole , kuma a karo na farko cikin shekaru shida da fara aikin sa ," bai taɓa rubuta hutu ba sai fa wannan karon da So ya jefa shi a damuwa ,! Dan haka ya zaɓi yayi ɗan nisa da inda ta taɓa zama da duk wani abun da ya shafe ta na ɗan wani lokaci ko zai samu ya danni zuciyar sa ya yakice ta baki ɗaya daga cikin tunanin sa ya fuskanci rayuwar sa ta gaba , cikin taka tsantsan da duk wani lamari na mata , haka yake fata haka yake buri. Ya gama tanadar kome da mahaifan su zuwa ƙannen sa zasu iya buƙata na kimanin watanni biyu a gaba , gefe guda bai ƙi ba , bai ɗauke kai ba , bai kuma yi fatali da marayun da yakaka ta wofantar ba duk da cewa ya so yin hakan da farko amma tausayi da ya riga ya zama bangare mafi kyau a cikin jerin halayen sa ya sanya shi gaza yin ko oho da lamarin Falmata da baby mama ,    toh meye laifin su ? me suka yi masa ,?  basu da laifin kome basu kuma yi masa kuskuren kome ba, su ɗin Raunana ne abun a taimakawa Duk da cewa ya ɗauke ƙafafun sa daga cikin saboda kiyaye zuciyar sa da tuno masa da yakaka da take yi , amma cikin tanadin da yayi akan tafiyar da zai yi bai manta Falmata da mama ba su ma ya tuna da su , Ya sayi Cartons na madarar baby mama zuwa daiper , wiper , da tarin kayan jarirai himili guda , Falmata kuwa cikin kuɗin da ya danƙawa Rahima yace ta raba uku ta bada kashi ɗaya ga Fatima , Bayan ya kammala haɗa duk wasu abubuwan da zai buƙata Zama yayi akan kujera ya miƙe ƙafafun sa aƙasa tare jingina kansa da fuskar kujerar ya ɗaga kan sa sama , " Tunanin da bai so shi ya fara , kafin kunnuwan sa su fara jiyo masa kukan ta char-char -char tana yi babu ƙaƙƙautawa , shiru yayi yana jin yadda tausayin ta ke lulluɓar sa ,  yasan ba kukan kome take ba illa kukan rashin jin ɗumin jikin uwa , Lumshe idanun sa yayi yana jin sunan da wani sashi na zuciyar sa ya ƙira yakaka da shi ,"muguwa ," Ji yayu kukan ya tsawaita , kuma kasantuwar dare ne tamkar a gaban sa take yi , har cikin ran sa yake jin kukan nata , dan haka ya mike cikin rashin kuzari ya sanya takalmun sa ," gami da yiwa cikin gidan tsinke ,  A tsaye ya tarar da su su uku , Falmata Rahima , Da kuma hajja mai wurya ,"  Baby mama tana rungume tsam a kirjin falmata hajja mai wurya da Rahima sunyi sunyi ta basu ɗiyar su gwada rarrashin ta taƙi , sai faman jijjiga ta take tana hura mata kunne , idan ban da kuka da mimmiƙewa babu abunda jaririyar take yi ,"   Meye same ta ? Yace da su lokacin da yake ƙarasowa inda suke ,"   Da sauri Falmata ta nufi inda taji tashin muryar sa ,"     Muryar ta tana karkarwar kukan da ta riga ta fara yin sa tun tuni , tace    Yaya dakta Dan Allah duba min Ita meya same ta ko bata da lafiya ne ? Tun ɗazu taƙi shiru ,     Bani ita yace yana karɓar ta daga hannun ta ba musu ta sakar masa ita , ta kafe inda take jin tashin muryar sa da ido , "    Jujjuya ta yayi a hannun sa , kafin yace ungo ta hajja rage mata waɗannan dogayen kayan ,   Zuruf Falmata tace kawo ta yaya dakta na iya cire mata , kuka take yi baza ta tsaya a cire mata a hankali ba , kar hajja ta ji mata ciwo ,"    Sakin baki hajja tayi cikin hasken falon ta dallawa falmata harara ,    Zata yi magana Dakta hamza yayi mata alama da hannu tayi shiru , Miƙewa falmata baby mama yayi,     Ga mamakin sa tsaf ta cire mata kayan jikin ta ta barta da diaper tana ta sharar ƙwalla , ta miƙa masa ita dudduba ta yayi ya tattaɓa cikin ta inda nan take ya gane cikin ta ne ya kumbura ,        Ɗaura ta a kafaɗa yayi a hankali ya shiga shafa mata baya yana ɗan jijjiga ta , ba'a fi mintuna huɗu ba ta fara fitar da iskar da ta cika mata ciki , a hankali kuma kukan ya fara lafawa , kafin mintuna goma ƴar jaririyar tayi bacci abin ta , Sauƙe ta yayi ya rungume ta a ƙirjin sa , yana kallon ƴar zagayayyar fuskar ta da take ruwan hoda dan fari , gashin da ya kwanta a gaban goshin ta har ya haɗe da girar ta , ,"irin na maman ta ya aina cikin ransa ,"    Da sauri ya miƙawa Falmata ita Ungo karɓe ta Fatimah , nan gaba idan zaki bata madara ki tallafo kan ta , sannan bayan kin gama bata ki ɗora ta akan kafaɗar ki ki dunga shafa bayan ta kar ki kwantar da ita sai kin tabbatar tayi gyatsa , sannan kar a bata madara da ya zarce ka'idar da aka umarta a bata , waye ke hada madarar ?   Ita take haɗa mata cewar Rahima Ita kuma ?  Tayaya zata auna ?  Meyasa ke bakya haɗa mata ? Kafin tayi magana Hajja mai wurya tayi wuf tace ,     Yo wannan yadda take ƙwalafacin ƴar nan da wa ta yarda ? Ko fa ɗaukar ƴar bata yarda ayi , koyaushe tana ƙunshe a hannun ta kamar lalle ,! Cikin siririyar murya falmata tace ina ganewa yaya dakta , idan na ɗibo madarar a cikin ɗan ludayin ɗibar madarar sai na shafe kan sai na zuba a robar bata madarar, sai nasa ruwan ɗumi dai-dai zanen layin na biyu ko ?      Hakane , haka zaki cigaba da yi mata     yace , yana kama hanyar barin wajen ,    Yaya dakta     Ta ƙira sunan sa .   Chak ya tsaya kafin ya waiwayo ta     Na'am Fatima Mun gode da kome , Mun gode da taimako, Allah ya ninka maka ya saka da Alheri,     Jim yayi kafin yace mata   Ameen Fatima , gobe zan yi tafiya ki min addu'a     Allah ya kiyaye hanya , Ya dawo da kai lafiya , Allah ya baka sa'a    Ameen Yaa Rabb Yace yana ƙarasa barin falon , cikin ran sa wani irin yanayi yake ji na taso masa , Ina ma ? Ina ma ? Kai ina ma daga bakin ta waɗannan kyawawan addu'o'in ke fitowa  ?           Washegari Ƙarfe bakwai na safe Doctor Hamza yayi wa mahaifin su Sallama bayan doguwar hirar da suka yi tun bayan sallar asubah ,  duk wata nasiha da yakamata tare da tunasarwa sai da yayi masa , A ƙarshe da ya miƙe zai tafi ya bishi da addu'o'in tsari da fatan samun nasara suka yi sallama , ya shiga motar sa yana barin gidan ɗauke da niyyar biyawa yayi sallama da Amne kafin ya ɗau hanya ! Ƙarfe tara ta sami colonel Youssouf  tare da colonel Tafeedah a babbar headquarter na soji da ke garin ,"Giwa barrack ,"  inda bayan ƴar gutuwar mahawar tare da gabatarwa aka haɗa su da gungun sojoji kimanin su goma sha biyu akan su raka su , a je a kwaso mutanen da colonel Youssouf yace sun ɓoye masa ƙanwar sa ," Hilux biyu ta soji ɗauke da bindigogin su suka yiwa unguwar su madam saly tsinke ,.    Tunda suka doso unguwar matasa da ma wasu daga cikin magidantan da  suke da tsoffin laifuka suka fara guje-guje , kasancewar unguwar kusan cike take da marasa ji ƙananu da manyan masu laifuka sai kawai aka hargitse da guje-guje , saboda sun san haka tsigau gungun sojoji basu kauce hanya su gangaro musu cikin unguwa ba shakka wani ne yayi wata ta'asar aka zo yin ram da shi , Basu kula kowa ba suka bi hanya ƙarƙashin jagoranci Conole Youssouf da yake hakimce gaban motar farko . Tun daga nesa madam saly da Ɗan liti da suke zaune daga cikin rumfa kan kujeru suna jajantawa juna game da asarar maɗuɗai da suke jajen sun same su , suka fara jiyo jiniyar motar sojoji ,"     Gefe guda kuma ma'aikatan tane baki ɗaya kowa na aikin sa , masu goge-goge da share-share na yi , ta ciki kuma masu wanke-wanke da haɗa ruwan barasar nayi .     Ɗan liti da ke karkaɗa ƙafa yana tsuma yace    Hmm ai ke dai saly fara bar tuna min ,"cin kazar daren farko ," ban son ko tunawa da yadda waɗannan magudan kuɗaɗen da Bala manci yayi mana ta leƙo ta koma da su , ai ƙwaranƙwasa da mun kama su da mun tsalleke kogin talauci , naira dubu ɗari tara fa saly fara ?  Kuma ke a ganin ki da mun biya masa buƙatar sa ba zai cikace mana ya zama miliyan bane ??    Kai dai bari liti wallahi ni sai yanzu nake jin takaicin gudun tsinannun yaran nan ƴan gudun hijira yaks da ƙanwar ta , ka ga wannan ƴar luɓu-luɓun ƙanwar tata ai ita ce irin wacce Bala ya nemi da mu kai masa , ƴar ƙwailar da take gaf da balallagewa , "   Uhun ni na tabbatar ke ce mai baƙar ƙafa saly dan duk wata harka indai ta kuɗi ce idan na haɗo da ke ban ganin falala a cikin ta , ƙwaranƙwasa da na sani da juwai me kala-kala na kaiwa harkar nan da yanzu tuntuni kuɗaɗe na sun nuna sun yi ligif a hannu na ,"dan nasan ko ramin kura ta shiga ta nemo irin wacce bala ya nema ,"    Wani kallon sheƙeƙe madam saly ta jefawa ɗan liti ,    Lalle kuwa liti , yo yaushe daren yayi nasa tuwo a ido ?? To idan ka fasa kaiwa juwai me kala kala harkar ka ta samun kuɗi nan gaba kai ba ɗan halak bane liti muna nan da kai zaka dawo da ƙafafun ka ni ɗuwawu ce dole a zauna da ni ,   Rama kallon banzan yayi ya murza yatsu,"suka bada sautin ," ɓas     Ni ce ma ke saly fara , nace ni ce ke , gaba asara baya asara ai wallahi , ki ji ni da kyau idan ido ya mutu kwalli bai tada shi , ke da kan ki dai kin san kome yanzu ba irin na da ba ne , anbar yayin 504 Yanzu 406 ce ke kada maza ahaayye ji min saly fara zata gwadan salon su na tsofin bariki ??      Ta buɗe baki da nufin maida masa martani suka ga ƙartin mazan da ke karta ta waje suna shigowa da gudu suna tsalleke katangar da take ta ƙarshen filin gidan, miƙewa su duka biyu suka yi , dai-dai da shigowar wani gabjejen ɗan busa hayaƙin da ya sha yayi manƙas da gudun ma da ƙyar yake wondan sa a hannu ,    kai idi meye ya faru na gudu ? Inji madam saly    Ta wajena ki arce kiyi ta kan ki idan ba gungun rundunar sojojin Nigeria kaf ne suke shigowa gidan nan ba ,"  Mts ɗan liti ya jaa tsaki yana komawa ya zauna ,    Zauna muyi hirar mu saly fara yanzu haka wannan na maliyan sha yayi tafi ƙarfin ƙwanyar sa , yazo yana mana subaɗaɗi , wai gungun sojojin nigeria ?  Ahayyee asha ruwa ayi tamɓele .    Anya kuwa ɗan liti baka zuwa ka dubo mana ko ƴan sanda ne ? Kasan su fa matsayi ta ne ba mutunci ne da su ba yanzun nan sai su chafke mutum su sha janin sa ,"   Bazai wuce su," Corporal garuje " ne suka zo samame ba suna neman na shan matala Kin fa san wata yayi nisa kum...         Kamar ɗaukewar wutar lantarki madam saly ta ji ɗan liti ɗif,"    Kan ta ankara ta ga gungun sojojin da suke ɗurowa cikin gidan , " cikin ta taji ya murɗa nan take laɓɓan ta suka ɗauki rawa ta gagara cewa ƙala ,"    Na ƙale , wallahi na ƙale , nayi surrender !    Ɗan liti ya furta haka yana kai guiyoyin sa ƙasa bayan ya ɗage hannuwan sa sama Kai tsaye sojojin suka dunga kutsawa  ɗakunan gidan suna wurgo mutanen cikin ɗakuna waje ta ƙarfin tsiya , cikin mintoci kaɗan sai ga mutanen gidan rankatakaf a filin gida ,    Kowannen su ciki ya ɗuri ruwa, sai waige waige suke , suna bin sojojin da suka saita su da bakin bindigogin su da kallo ,"cikin son sanin meke faruwa ? Wanne laifi suka yi ? Amma ba halin tambaya soboda tsoro  Tsakiya colonel Youssouf ya fito cikin muryar sa mai amo da yake buɗe ta ya haka a bakin daga yace    Ina yarinyar da kun ka boye a cikin gidan nan ? Ina take ? Ina Kun ka kaita ? Kuyi gaugawar fiddo ta kafin harsashai su sauƙa a kawukan ku baki ɗayan ku ,      Cikin maƙyarƙyatar muryar da tsoro ya riga ya bayyana kan sa a ciki ɗan liti yace    Wallahi Tallahi ranku ya daɗe ni ban san kome ba , ni yanzu shigowa ta gidan ma karbar saƙo wallahi ko jinjirin kiyashi bazan iya cutarwa ba bare ɗan mutum , ɗan mutum ma irin wannan mai darajar dan ....    Dukan da sojon kusa da shi ya kai masa da ƙafa ya sa shi sakin ihu tare da zaman ƴan daɓaro a ƙasa ,   Matsowa Youssouf yayi , kan madam saly    Kin samo ta ko kouwa a ah ? Zaki fiddo ta ko kouwa sai kin ji ƙamshin mutuwa ,??     Idanun madam saly da suka sake shigewa ciki saboda tsoro suka kawo ƙwalla,    Wallahi ranka ya dade na duba ,  mun duba mun cigita , mun yi neman saƙo da lungu amma ko wanda yace ya ji ɗuriyar su ma ita da ƙanwar ta bamu ji ba , wallahi ranka ya daɗe ba ni na kori yarinyar nan ba raina yana son ta ina ƙaunar ta ita da abun.... Marin da ya ɗauke ta da shi ya hana ta ƙarasa dogon labarin ƙanzon ƙuregen da ta kwaso ,"   Ku musu duka ku kai su mota mu wuce da su barrack , idan sun ɗanɗani azaba zasu faɗi inda take , " cewar Yaoussouf   Kamar jira suke suka fara ƙwallo da su nan take guri ya ruɗe da ihun matan banza da kururuwar ɗan liti da ya buɗe maƙogoro yana zurma ihu tamkar ana watandar tsokar jikin sa , ya buɗe muryar sa ta asalin garjejen namiji ,"    Kora su suka fara yi waje da shirin tafiya da su barikin su na soji ,"   Nan fa idanun Yagana ya fara raina fata wacce ta sha manyan bulalai huɗu ,    Ita tasan aka kai ta wannan barikin sojin sai ɗan buzun ta ,"  ta tsoraci soja ba kaɗan ba domin ta ga irin yadda basu ɗauki kisa a bakin kome ba ,      Bulalar belt ɗin da wani soja ya sake sauƙe mata a gadon baya yana tunkuɗa ta ita ta gigita ta ,"   Wayyo Allah bayana , fatar bayana ta sulluɓe , dan Allah ku tsaya wallahi na san inda take zan kai ku , zan kai ku Dan Allsh kuyi haƙuri kar ku tafi da ni ,     Matsowa gaban ta yayi ya bar chasa madam saly da ta riga ta fara galabaita da bulalar soji ,     Kin ka ce kin san inda take ?  Tana ina ? Ki kai ni yanzu - yanzu idan kin ƙi zan harbe ki ,"     Muryar ta tana sarƙewa tace Nasan inda take kuma ma ai ƴar uwa ta ce zan kai ku yanzu , Dan Allah kar ku ji min ciwo kar ku tafi da ni ,wallahi nasan inda YaKaKa take ," Finciko ta yayi ya miƙar ta tsaye , muje ki kai ni      Yace yana tunkuɗa ta gaba , kafafun ta ko takalmi babu ,    Ku cigaba da tsare su , idan mun same ta zan sanar da ku ta téléphone sai ku ƙyale su idan bamu same ta ba zaku zo mouna da su barrack , Ɗaya daga cikin motar suka hau , Yagana da Youssouf da Tafeeda ,   Ki gouda muna hanya," yace da ita Ba'a yi wata tafiya mai nisa ba Yagana tace a tsaya ga gidan     Tana yi musu nuni da gidan Amne , Su suka fara fitowa shi da Tafeda suka tasa ƙeyar yagana kai tsaye suka sanya kai cikin gidan .     Amne tana kishingiɗe akan ƴar daddumar ta tana shan hantsi ta ga tsayuwar sojoji akan ta ,"    Miƙewa tayi zaune tana kallon su a tsorace ,    Wannan ce ta ɓoye su Yagana tace haka tana nuna Amne da ɗan yatsan ta ,    Da sauri ta miƙe tsaye , Ranku ya daɗe lafiya ?   Wanne laifi nayi dan Allah ? Yarinyar da kin ka boye zaki fiddo mana ita yanzu mu tahi da ita ,ƙanwa ta ce ,    Wacce yarinyar ?   YAKAKA Yagana ta bata amsa tana matse ido Zuciyar Amne ta buga da ƙarfi dan razana ƙwarai ta gane yakaka yarinyar da ta mutu wurin haihuwa , ƴan gudun hijirar da ɗan ta ya taimakawa yake riƙon su a gidan su , ganin jami'an tsaro suna neman ta yasa hantar cikin ta kaɗawa , anya baza su harbe ta ba idan ta gaya musu ai wacce suke nema ta mutu ?? Ko su tafi da ita barikin su na soji su wahalshe ta a banza , bata da mai karbo ta , ɗan ta yau-yau yayi tafiya , ya bar garin , dole tayi taka tsantsan kar ta ɗaure kan ta ! Mahaifin su Hamza babban mutum ne ba abu mai sauƙi bane a tozarta shi musamman ma da ta san basu yi wani  mummunan laifi ba , tana da yaƙinin idan ta sada su da shi kome zai zo da sauƙi , shi zai iya musu bayani su fahimta ,      Ni ba nice mariƙiyar su ba riƙon kwana ɗaya jal nayi musu , a halin yanzu suna gidan mariƙin su , zan iya kai ku gidan na dawo ?   Ta ƙare jawabin ta da sigar tambaya ,?    Ki gouda mana gidan , idan har kin san gaskiya kin ka faɗi ,"   Gaskiya ne wallahi , muje na kai ku , Babu Ɓata lokaci Amne ta kai su har Unguwar su Doctor Hamza ta nuna musu gidan daga nesa , Kuna iya komawa muhallin ku Tafeeda yace da su, Youssouf zai yi magana , ya masa alama da yayi shiru ,"     Gudu-Gudu Yagana ta tare mai napep ta shiga , sansanin ƴan gudun hijira zaka kai ni ," tace da shi tana waiwayen bayan ta ,     Ta ɗan madubin gaban napep ɗin ya dube ta , wanne daga cikin sansanin ƴan gudun hijirar zan kai ki ??    Na hanyar bulunkutu tace da shi , Cikin ran ta tana kitsima gara ta koma sansanin ƴan gudun hijirar inda samun ta zai yi wahala , zata ɓace a cikin dubunnan ƴan gudun hijira ƴan uwan ta domin ta san ta yarda ta bari  wannan sojan ya san da haɗin bakin ta aka gudu da Yakaka har wani garin da ita kan ta ma baza ta ce ga sunan garin ba , bata da hanyar saduwa da samy baby , toh fa tasan ba abunda zai hana shi harbe ta har lahira ya kashe ta !    Tattaki suka fara suna nufar gidan da kowanne cikin su ke yiwa kallon sani ,     Kusan a tare suka ce da juna wannan ai gidan da munka zou biki kwanakin baya ,"       Babu shakka shine Yarima Youssouf ya amsa , Maigadin gidan ne ya tare su , cikin ladabi ya gaishe ya ɗora da tambayar su ina suka nufa ?   Suka shaida masa gurin maigidan suka zo ," nan ya shaida musu zai shiga ya sanar da shi zuwan su , har youssouf zai yi magana , Tafeeda ya sake dakatar da shi , bayan wucewar sa yace da shi ,"     Ɗan ouwa mu bi kome a sannu , kar muyi garaje .   Bai ce da shi kome ba , suna tsaye maigadin ya fito yayi musu iznin shiga gidan ƙarƙashin jagorancin sa ," Har cikin falon yayi musu jagora , prof yana zaune suka shigo bayan sun sunce ƙwafta-ƙwafatan takalman su daga waje ,    Da kallon rashin sani yake bin su bayan sun gama taƙaitatciyar gaisuwar da ta shiga tsakanin su ,"     Samari daga ina kuke ? Ban shaida fuskokin ku ba !     Ɗan jim suka yi suna tattaro nutsuwar su , kafin Tafeeda da shine ya tsara kome yace    Baba munzo neman watta ɗiya da anka ce kana riƙo sunan ta Yakaka , " wannan mijin ta ne ,    Ya ƙarasa zancen yana nuna youssouf     Ɗan jim prof yayi, wacece yakaka ? Ko dai yarinya ƴar gudun hijira ? ,' Yaya kamannin ta yake ? Kuma a wanne yanayi take ,"    Doguwa ce fara , tana da tsago a fuskar ta , sannan , sannan kuma tana ɗauke da juna biyu ,      Youssouf ya ambata Kaine mijin ta ?  Prof yace da shi fuskar sa na nuna jimami ,"   Ni ne baba   Ya amsa   , cikin zuciyar sa yana fatan tambayoyin su tsaya iyaka nan , tare da zaƙuwa da son a ƙira masa ita ya gan ta , Allah sarki ashe ma ƴar hijira ce ,    Tunanin sa ya tsaya chak lokacin da yaji prof yace     Yaro ina baka haƙuri tare da tunasar da kai akan cewa duk wani mai rai mamaci ne , yarinya yakaka ƴar gudun hijira ta rasu a wajen haihuwa bayan riƙon su da muka yi a gidan nan tsawon watanni bakwai , ta rasu ta bar ɗiyar da ta haifa tare da ƙanwar ta da muke riƙon su tare ... Ji yayi wani irin yanayi mai kaifi yana ratsa zuciyar sa wanda ya zarce kaifin tsoro ko firgita , tsintar kan sa yayi a hali na shuɗewar tunani na wucin gadi , jikin sa a take ya ɗauki rawa , da wannan yanayin ya watsa idanun sa kan Baba prof ,"    Yarinya yakaka ta mutu ? Ta mutu a wajen haihuwar abunda ke cikin ta ? Ta mutu bamu gana na nemi yafiyar ta ba ?  Ta mutu ban gyara kuskuren da nasa muka aikata tare ba ? Ta mutu Alhalin ban nuna mata godiya  ta akan irin taimakon da ita take tunanin ta mun ba ? Meyasa ta Mutu ta bar min nawi mai girma bissa kaina ni kaɗai ?    Tafeeda ne ya riƙo shi ganin yadda yake surutai kusan bai cikin hayyacin sa , tabbas shi da kan sa ya ji mutuwar  yarinyar , kome kuma ya kunce masa , zuciyar sa kuma ta raurawa , Kayi hakuri yaro mutuwa na kan kowa bari na ƙira a kawo maka ɗiyar ka , ƙanwar ta ma ta zo ku gaisa ,"   Waya yayi cikin gidan akan a zo da Falmata da baby mama ," Ya maida hankalin sa kan su Youssouf da tafeeda yana nazartar su , akwai tambayoyi dayawa da yake son yi musu ba wai dan bai yarda da su ba , sai dan a farkon kawo yarinyar gidan Hamza ya sanar da shi mijin yarinyar ya mutu boko haram sun kashe shi , sai kuma ga shi yanzu ya ga jami'in tsaro a matsayin mijin ta ko daman ɓata yayi ba mutuwa ba tsawon wannan lokacin ? Shigowar Falmata riƙe da mama tare da rahima , shi yasa biyamuradi Youssouf ɗago kan sa ,"     Idanun sa so suke su ga ɗiyar , so yake ya samu rangwame ta hanyar fahimtar bashi da alaƙa da ɗiyar da aka samar ta hanyar banza wacce zuwan ta yayi sanadin mutuwar mahaifiyar ta me tarin rashin galihu , bai so lamuran sa su sake munana ,    Sai dai wani yanayi da ya tsinka jinin jikin sa lokacin da hasken fuskar ƴar jaririyar da ya ɓanɓare daga hannun falmata ba tare da ya jira sun ƙarasa shigowa falon ba yayi tattaki da sassarfa ya taro su ,     Yanayin mai ƙarfi ne da bai taɓa jin kwatankwacin sa ba da ɗai duniya , Jin sa yayi a wani yanayi wanda ya so ya saɓawa wanda yake cikin sa kafin ɗora idon sa akan ƴar da yaji ya gaza gane wacce matsaya yayi mata a halin da yake ciki ,    Kallon ta yake tamkar yana son ganin abun da ke lulluɓe cikin fatar jikin ta , kallon da yake mata ya sa duk wata suffa tata jeruwa cikin tunanin sa tana juyawa tare da girma mataki-mataki har zuwa lokacin da kammanin ta da mahaifiyar sa suka gama fitowa tsaf , tamkar kobo da kobo ,      Bai san lokacin da idanun sa suka samar da ruwan hawaye ba sai kawai ganin ɗigar su yayi akan fuskar ta , wanda ya nutsar da idanun sa kai babu shakka yana iya kallon ƙofofin gashin jikin ta ,    Sauƙar ruwa a fuskar ta ya sanya ta buɗe idanun ta a hankali ta wara su akan sa , fes !  da shi ma ya sake ware nasa idanun tare da ɗage duk girar sa biyu abun da ya kan yi idan yana cikin yanayi na shauƙi , Yamutse fuskar ta tayi cikin salon su na rikicin jaririyar zata yi kuka ,       Da sauri ya ɗago ta zuwa dai-dai fuskar sa ya sanya kan karan hancin sa yana goge mata ƙwallar sa dake kan kumatun ta da yake zaton ita zata sa ta kuka ,    Ai kuwa tamkar ya kunna ta sai kuwa ta sa kuka ,    Kukan ta ya zo dai-dai da fashewa da kukan falmata wacce da kyar Rahima ta banbare hannun ta daga cukumar da tayi wa rigar Youssouf , cewa take wanene anan ? Rahima waye ya kwace min baby ? Ka bani ita dan Allah ka bani ita kar ka sa ta kuka ?  Kai waye , ? Rahima kika ce min Baba ne yake ƙiran mu ,? To waye ne ya karɓe min Yakaka na ?   Muryar prof ta sa ta ɗan samu nutsuwa har ta sassauta riƙon da ta yiwa youssouf , rahima ta samu nasarar janye hannun ta ,   Amma kukan yarinyar da take jin sa kamar ɗigar narkakkiyar dalma ya sa ta kasa tsayar da kukan ta , "         Ganin kukan ta yayi yawa ya sa Tafeeda tasowa ya dafa kafaɗun Youssouf , yana kallon fuskar sa , muryar sa babu ƙarfi sakamakon halin da ya ga Youssouf ɗin ya shiga tunda ya ɗaura idanun sa kan ƴar , yana nufin ɓullowar wani gagarumin lamari Masarautar Maradi . Ɗan ouwa bada ɗiyar nan ga mariƙiyar ta , ga ta sai kuka take , ! Dauke idanun sa yayi da kyar daga fuskar ƴar ya mayar kan Tafeeda , da wata muryar da bata da amo yace ,"   Ɗiya tawa ce Tafeeda , wagga Ɗiya jini na ce , Ɗiya ta ce , A yau ni Uba ne , Uba ne ga wagga ɗiya da tsautsayi tare da kaddarar zuwan ta duniya ya sa kome ya faru kamar yadda ya faru ,"   Ɗan satar kallon prof , Tafeeda yayi yaga yadda hankalin sa baki ɗaya ke kan su , amma kasancewa falon me girma ne da ƴar tazara a tsakanin su ,    Wallah ka lura Ɗan ouwa idan ba hakka ba kana iya ɓata mouna kome , Hannun sa ya kai da nufin karɓe ƴar daga hannun sa , wata irin zamiya Youssouf ɗin yayi ya janye ƴar jaririyar sosai zuwa cikin jikin sa ," Baka ganin kuka take ?? Ka bari na lallashe ta ,   Haɗiye firgicin sa Tafeeda yayi , ka bada ita Yarima uwar goyon ta zata mata lallashi , akwai abubuwa dayawa a gaban mu ,    Ina uwargoyon ta ? Yace yana mayar da duban sa kan su Falmata da duk budurin da tayi na cukume sa da kalmomin ta duk bai ji su ba , ruɗanin da yake ciki ya toshe masa kunnuwa daga barin jin hayaniyar ta ,     Da ɗan yatsa Rahima ta nuna masa Falmata wacce tayi shaɓe-shaɓe da hawaye sai ajiyar zuci take ,   Ga ta nan , Matsowa yayi , ya miƙa mata ƴar    Karɓe ta , ki kula da ita kar ki bari kome ya cutar da ita , kar ki bari tayi kuka ban lamunta ba ,"    Hannun ta miƙa saitin inda take jin hucin sa , ta karɓi ɗiyar tana jin wani sanyi na ratsa zuciyar ta yana kore tunanin da zuciyar ta ke son kawo mata akan kamar ta taɓa jin amon murya kwatankwacin wannan ,! Da kallo Rahima ta bi shi , kamar shine ? Kamar fa shine na jikin hoton cikin kayanYakaka , babu shakka ma shine ,"    Ku koma ciki Rahima , prof yace ga su ,"    Toh , suka ce suna kama hanyar barin falon ,"     Youssouf zai magantu , Tafeeda yayi saurin yunƙurowa yana faɗin ,   Mun gode Mun gode Baba , Allah ya saka da Alheri ya bada ladan Taimakon da kayi mana , yanzu zamu koma saboda a bakin aiki muke amma muna dawowa cikin kwanaki biyu masu zouwa da yardar Allah ," Ameen toh babu kome Allah ya nuna mana kwanaki biyu masu zuwa Allah ya ƙara muku haƙurin jure rashi, idan kun sake dawowa zamu yi magana ,.. Youssouf zai yi magana ,   Tafeeda ya sake katse shi yana jan hannun sa    Ɗan ouwa tashi mu tafi , Jaan hannun sa yayi suka fito daga gidan suna fitowa Youssouf ya zare hannun sa daga na Tafeedah , A tare suka haɗa baki wajen tambayar junan su ,! Ɗan ouwa meye haka kake shirin yi ? Kana nufin nan zan tafi na bar ƊIYA TA ?    Hannun mutanen da ban san su ba ? Kallon baka da hankali Tafeedah ya yi mass kafin ya fara taku ya nufi wajen motar su , ',kazo muje muyi magana a tsanaki ,    Ran sa bai so ba ya faɗa motar ya shiga Tafeeda ya fara ƙoƙarin tada motar lokacin da yake magana da sojojin nan akan su bar su madam saly an samo inda yarinya take ,"  ya sauƙe wayar yana hawa kan titi , Da fitar su Prof ya ɗaga waya ya ƙira Doctor Hamza bayan sun gaisa , yace      Yanzu mijin yarinyar nan ƴar gudun hijira mai rasuwa ya bar nan gabana tare da ɗan uwan sa , ka ga ikon Allah ashe shi bai mutu ba , ya zo ya ga gan ta tare da ƴar sa yana...    Wani mummunan cin birki da Doctor hamza yayi wanda hatta prof sai da yaji ,   Subahananlahi , Hamza ban hana ka ɗaukar waya alhalin kana tuƙi ba ? Da fatan dai baka yi haɗari ba ? kana jina ?    Muryar sa ƙasa ƙasa ya amsa bayan ya ɗauke kan motar zuwa gefen hanya bakin daji ya tsaya , Ina ji Baba , a bashi ƴar sa tare da ƙanwar matar sa ya tafi da su kar su sake dawowa Baba ,"    Jimm prof yayi , Kafin yace Toh babu kome idan sun nemi hakan ai sai a basu daman ai hakan ya kamata , ka dunga kula hamza ka daina ɗaukar waya alhalin kana tuƙin mota , kana ina ne yanzu ?    Ina jigawa Baba , insha Allah zan kula baba , ka min addu'a baba , zamu yi magana idan na isa .   Toh Allah ya tsare hanya daga ka isa ka sanar da ni ,   ,"To ," yace yana sauƙe wayar Cije gefen leben sa yayi , watau dai kome gaskiya ne , ga shi nan duk yadda suka shirya yana faruwa daki-daki , watau har sun yi auren ta turo shi ya zo ya ɗau ƴar sa da ƙanwar ta ,    Zuciyar sa tayi duhu , me na miki da zaki yi wasa da zuciya ta irin haka ? Ashe sakayyar da zaki min kenan ? Wani irin kishi mai ɗaci yake ji a ran sa , shan alwashi yake daga yanzu bai ƙauna sake jin ko me suna irin nata , bai ƙaunar sake jin duk wani abu da ya shafe ta , bashi da wani sauran uzuri da zai iya bata kariya da shi , ya yarda ya amince ta yaudare shi . Tada motar yayi a hankali ya hau titi , yana nisawa cikin tunanin mace a yau ! Sojojin nan basu bar su madam saly ba sai da suka sake chasa su yadda ran su ke so ," Ah soja birgimar hankaka ne fa ?      Suka yi ficewar su suka hau motocin su wasu a tsaye a bayan hilux wasu a zamne , suka yi tafiyar su ," illahirin gidan a ruɗe yake da kururuwar matan da aka lallasa , sai ɗuruwa ake ganin su ana tambsyar me ya faru ? Me suka yiwa sojoji ? Ɗan liti wanda muryar sa ta dashe saboda tsabar ƙwarmato , ya dubi madam saly wacce bakin ta ya kumburo yayi suntum sakamakon haƙorin ta ɗaya da ya fita ,"   Cikin dusashiyar muryar sa yace saly fara yau wacce rana ce ? Kuma a wanne wata muke nawa kuma ga watan ??    Da ido kawai madam saly ta bi shi tana jin yadda raɗaɗi yake ratsa tsokar jikin ta ta ko'ina gefe guda ga bakin ta da take ji kamar an cusa garwashi ,"    Ya cigaba , Na rantse ki rubuta ki ajiye ido na idon wannan tsinannan yarinyar yagana sai dai uwatta tai naƙudar wata , wai ace kana zaune da makashin ka baka sani ba ?  Ashe tuntuni ita ta san ana nan ana shirin far mana da yaƙin basasa ,amma tayi funfurus ta ƙi faɗa mana bare muyi ta kan mu ,ki tsoraci ɗan adam ƙuzazje mai tafiya da ƙafa biyu saly fara , wai yanzu ace tsawon lokacin nan ashe shegiyar yarinyar nan mai kama da takanɗa ta san inda yaran nan su yaks suke , shine bata taɓa yunkurin faɗa ba "ko daya ai yake hannun hagu ba baƙon duwawu bane ,"duk jirgi ɗaya ya kwaso su ," to ƙwaranƙwasa ba'a daki bulus ba, farautar ta zan shiga yi ba dare ba rana ," wayyo wayyo ni liti du mazauna na sun yi tsami sun ɗuri ruwa , saly gane min ko dai farfashewa mulamulai na suka yi ?    Ya juyo mata duwawu , Kawar da kan ta tayi tana miƙewa da kyar ta nufi cikin gidan tana aiyana irin mummunan matakin da zata ɗauka akan Yagana , ai ita ba'a zubebeniyar ƙwaryar rashin mutunci da ita mutum ya kwashe ƙalau ," ***** Bayan komawar Biyamuradi Youssouf tare da Tafeeda ɗakin hotel , kowannen su shiru yayi yana saƙa cikin zuci , Ta bangaren Youssouf abu biyu ne zuwa uku , na farko mutuwar Yakaka da ta girgiza shi ta kuma bashi tsoro , ya wanzu yana tunanin da yanzu shi ne fa ya mutu ? Me zai cewa ubangijin sa akan tarin laifukan da ya wanzu yana aikatawa , tausayin ta yaji yana ninkuwa a ransa , tare da alwashi da yake ɗaukarwa kan sa na wanzuwa yana yi mata addu'a neman gafarar ubangiji har zuwa tsayuwar nasa numfashin , Ƙaunar ƴar jaririyar da kafin ɗora idanun sa akan ta suks tsara da shi da tafeeda akan cewa ko abun da aka haifa ya/ta nuna wasu alamu a halittar sa/ta dake nuna cewa nasa ne baza zai amince ya dangantar ɗa/ƴar da cewa jinin sa ba ne , kasancewar ya riga ya faɗawa Tafeeda yakaka ƴar talakawa ce sun san cewa ba wani tsananta binciken su gwajin jini a tsakanin sa da ɗa/ƴar da aka haifa za'a yi ba , dan haka suka tsara zasu barwa yakaka abunda ta haifa amma zasu taimaka mata tsayin daka kamar yadda tun farko Biyamuradi youssouf ya tsara , Sai dai fa kome ya sauya ya birkice masa lokacin da ya rungume ƴar sa a ƙirjin sa , ya ɗora idanun sa akan ta kamannin mahaifiyar sa duk suka bayyana kan su a halittar ƴar , ta buɗe idanun ta ta kalle shi , so irin na tsakanin ɗa da iyaye yayi tasirin sa cikin ƙudurar ubangiji , wani irin so mai yawa mai tafe da tausayi da tsantsar zallar ƙauna marar gauraye irin ta iyayen da suke da matuƙar ƙwalafaci da ƙawa zucin ƴaƴan su , suka taso suka lullube zuciya zuwa idanun YARIMA YOUSSOUF ABDUL-AZIZOU BASKORE Yaji zai iya sadauƙar da kome da ya mallaka domin ya tsira da ƴar jaririyar ƴar da tayi rashin ɗumin uwa tun daga ranar zuwan ta duniya , rashin maihaifiya a tare da ita ya kassara illahirin gaɓɓan jikin sa , ji yake ina ma yana nan ranar da ta zo duniya alhalin uwar ta bata tare da ita , da tun daga ranar zai fara gwada mata ƙauna da tattali mai tudu biyu irin na uwar ƙwarai kuma jajirtattcen uba , tausayin ta yake , tausayin da bai taɓa jin yayiwa wani mahaluki irin sa ba , bai ƙi ba ace tun daga ranar haihuwar ta har zuwa lokacin da zata mallaki hankalin kan ta ƙirjin sa ya zama wajen kwanciyar baccin ta , so yake yayi mata rumfa ya zama mamar ta , kuma baban ta , ya zama ya cikace gurbi na duk wani makusanci da yaro zai nema cikin rayuwar sa na ƙuruciya , bai son ta tashi cikin maraici , tunanin hakan kawai na sauke ƙwalla a idanun sa , yana kuma katange tunanin sa daga duk wani ƙalubalen da kasancewar ƴar a rayuwar sa zai iya samarwa , kou yanzou baby ta daina kuka ? Ya tambayi Tafeddah wanda ya rafka tagumi hannu biyu ya zurfafa cikin tunanin yanayin da ya hango da alamomin da suka bayyana kan su ga Yarima daga lokacin da ya ɗora idanun sa kan ƴar jaririyar da a yanzu yake hango alamun zamantowar ta barazana ga farin cikin mutane da dama da suke kewaye da yariman , shi yasan wanene youssouf , a lokuta da dama ba sai ya masa bayani ba yake fahimtar abunda ke cikin zuciyar sa , sai dai ya san wannan karon Yarima zai zo da wani Al'amari mai girma muddin ya nuna son ƴar ta tsaya tare da shi cikin rayuwar sa , Abunda hakan zai haifar ba abune mai daɗi ba , bai son ko tunawa , yau ace yarima youssouf ya doshi cikin masarauta tare da ɗiyar da ya haifa ba tare da amre ba , al'amura zasu rinchaɓe, kai ka kawo yake cikin tunanin sa yana son samar da hanyar da zai bi ya dakatar da yunƙurin yarima ya bar ɗiyar nan a inda ya dace ta zauna,    Tunanin sa ya katse lokacin da yaji youssouf ɗin nayi masa magana ɗagowa yayi ya dube shi    Me kake faɗi yarima ban ji ba ?   Ɗiyar nan ko ta daina kuka yanzou ?  Wacce iriyar madarar jarirai ake bata ?    Sasarere Tafeeda yayi yana kallon youssouf ,   Anya kou ranka ya dade yarima ba'a bar batun jaririyar nan haka nan ba ?baka gani Allah ne ya doube mu ya kawo hanyar da zamu samu masalaha akan wagga lamari ya kawar da uwar ɗiyar domin mu samu mafita ," abun da ni nake gani shine ka bar ɗiyar nan wajen masu riƙon ta tunda ba mu riga mun sanar da wani abu da ya shafi asalin mu ba ga mutanen nan ba, sai mu juya baya mu tahi abun mu ba tare da kowa ya san inda za'a same ka ba , ta iya yiwuwa ka dunga yin aike ta wata hanya mai nisa wadda zai dunga isowa ga ita ɗiyar nan , domin fa ka sani ita wannan ɗiya babbar barazana take a gare mu yarima da ma masarauta baki ɗaya , ko kouwa me kake tounani ne yarima ? Ko kouwa masalaha bata zou mana ba ??      Ya ƙarasa zancen yana kwantar da muryar ganin yadda Youssouf ɗin yake masa wani irin kallo mai karfi  dake bayyana ɓacin ran da yake cikin ran sa ,    Tafeeda me kake faɗi haka mai kaushi , kana nufin na bar ɗiya ta jaririya nan nigeria hannun mutanen da ban sani ba ? ƙaƙa kake son rayuwar ƴa ta ta kasance cikin wahala tare da rashin galihu ? Baka tounanin tarihi zai maimaita kan sa ga ɗiya ta , rashin galihu yasa ta faɗa kwatankwacin halin da mahaifiyar ta ta shiga har ya zama silar faɗawar ta halin da ya zama silar samar da wagga ɗiya ? INA SON ƊIYA TA TAFEEDA , DOUNIYA ZATA KASSANCE TARE DA NI , DUK RUNTSI NI AI MAHAIFIN TA ,      A hasale Tafeeda ya miƙe tsaye Amma ka san ita wagga ɗiya take ba ta halali bace  kou ? Ita ɗin baka samar da ita ta tsafatataciyar hanya ba , ita ɗin barazana ce ga martabar iyayen ka da dangin ka baki ɗaya , barazana ce ga hawan ka ƙaragar mulkin masarautar mu , ƙazanta ce ita wacce ya kamata ka ji kunyar bayyana ta ba.....   tsawar da Yarima Youssouf yayi masa ya hana shi , Kome zai yanke tsakanin mu idan ka sake touzarta ɗiya ta Tafeeda , ita ɗin batta da laifin kome , ni ai nine za'a hukkunta , ita wagga ɗiya bata tare da dauɗar kome , ita ai abun a tausayawa ce , ita ce kaddara ta Tafeeda ina roƙon ka da Allah ka taimaka mouna ni da ɗiya ta , ka tsaya tare da ni bisa lamurran ta ni nasani me tarin laifuka ne , ka duba wnnan ɗiya mai tarin rauni ,     Yarima youssouf ya ƙarasa zance tare da share ƴar siririyar ƙwallar da ta sauko masa ,    So yake ya samu mai taya shi son ɗiyar sa , so yake a bashi karfin guiwar tsaya mata , tafeeda yana da muhimmanci cikin rayuwar sa bai son ya juya masa baya a wannan gaɓar ,    Tare da wani irin yanayi yake kallon sa , bai son tausayin sa da ya fara ji ya rinjaye sa har ya taya shi aikata abunda yasan zai cutar da shi mummunan cutarwa , zai kawo tsaiko akan cigaban rayuwar sa , idan yayi haka shi yasan bai kyauta ba Amintaka bata cika ba, kuma hatta shi fushin iyayen yarima sai ya shafe shi ,  kai shi fa basshi da ƙwarin guiwar da zai bada goyan baya ga yarima a wannan gaɓar ," Yarima idan ka ɗau ɗiya jaririya irin wannan ka tahi da ita zouwa ina ?    Zan yi amre na bada riƙon ta ga maimounatou zata riƙa min ita ,"    Kana da tabbacin ƴar sarkin agades ɗiyan gata irin ta zata yadda tayi maka riƙon ƴa ?       nakan iya haƙourewa dagga amren ta muddin batta riƙon ɗiya ta.   Murmushin takaici tafeeda yayi kace da maimartaba da hajiya umma , da ƴan uwan ka me ??   Kaddara ta ce ta zou a haka , nasan umma zata fahimce ni ta fahimtar da maimartaba ƴan uwa zasu min uziri da afouwa  ,"   wanne irin tanadi kake tounanin maƙiya zasu yi ta hanyar ɗiyar nan su kawo naƙasu cikin rayuwar ka tare da lalata mana sunan masarauta ? Maƙiyi shi ai kullum maƙiyi ne , shi kuwa jajirtatcen namiji badda maƙiyan sa yake , gƴaɗa kai tafeeda yake yana iya hasaso gingimemen rikicin da Toussouf yake neman tsunduma kan sa cikin rayuwa ,    Allah shi badda sa'a yarima Amine ! yarima ya amsa yana jin daɗin ganin kamar tafeeda ya sauko zai goya masa baya ,       Yaushe zamou kouma ka ga ɗiyar nan ɗan ouwa ?    Gobe iwar hakka na hantse a ƙassa ta ta haihouwa ,    Gobe kake koumawa ɗan ouwa ?   toh zaman me zan yi a nan na baro aiki na ?  Gobe da iznin Allah nake koumawa .   Allah shi kaimu , Yarima Youssouf yace yana ƙarasawa gaban window ɗakin ya yaye labulen yana kallon rana da tayi yamma take gaf da tafiya ,    Ran sa cike taf da son sake ganin fuskar ɗiyar sa ....!!!              [7/9, 4:43 PM] +234 803 559 8589: Fikra writers association Mafari ....... Hargitsin Rayuwa . Umm'muaz 29 TUN RAN GINI RAN ZANE Washegari da misalin tara na safe , jirgi ya ɗaga da Tafeeda zuwa birnin Lagos inda ta chan zai wuce ƙasar su ,   Dukkanin su shi da Biyamuradi babu mai isashiyar walwala suka yi sallama , alhalin basu kai ga cimma matsaya guda kan matsalar su ba , Duk da cewa bangaren youssouf ya ji kaso sittin cikin ɗari na damuwar sa ta tafi , saboda ya bayyana ta ga aminin nasa , ya kuma san Tafeeda zai yi duk yadda zai yi ya ga ya dai-daita kome a gida kafin komawar sa  , yanzu babbar matsalar sa ita ce rayuwar ɗiyar sa , A daren jiya kwana yayi yana dogon nazari akan yadda zai yi ya ga ya bata ingantatciyar rayuwa ba tare da gurbatatciyar hanyar da aka samar da ita ta zama ƙalulabe a gare ta ba , da mutum yana iya sauya kaddarar sa da a daren na jiya ya juya , ya gyaro hanyar da aka yi ƴar nan ta sa ta zo duniya , amma ya riga ya san bakin Alƙalami ya bushe , hakan ya sa ya ɗau ƙuɗirin zai jajirce akan duk wani ƙalubale da shi zai iya cin karo da shi cikin rayuwar sa wajen ganin ya inganta tare da kyautata rayuwar ɗiyar sa ta FARKO a duniya ," Tafeeda kuwa ya bar ƙasar ran sa cike taf da tunanin yaya zai yi yaga ya boyewa hajiya umma musabbin shiga damuwar yarima ?  Ya zai yi ya boye mata irin mummunan aikin da yarima ya aikata ? Yaya zai boye mata samuwar wata haramtatciyar ɗiya daga tsatson ta ? Kome yana neman kubce masa , shi ya kasance a tsakiya ne , ɗan aike ne shi , sai dai saƙon da zai koma da shi a yau me nawi ne wanda ya fi ƙarfin fitowa daga kan harshen sa , Cikin awanni (2) da tashin jirgin su daga Murtala Mohammed International Airport Lagos, Ya samu dira a Diori Hammani International Airport Niamey , duk yadda ya so ya tsaya wajen 'ubbo' su gaisa kamar yadda ya tsara , ya gagara saboda rashin nutsuwar zuci , Allah-Allah ya ke ya samu isa wajen hajiya umma ," Jirgin da zai sada shi da Maraɗi kai tsaye ya hau , yana isa gidan su wanka kawai yayi ya sauya kaya ,ko abinci bai duba ba ya yiwa fada tsinke , nan ya nemi iso ga hajiya umma , aka yi masa ba tare da jinkiri ba ,"      Bayan ya gaishe ta yayi shiru yana son samun ƙarfin guiwar faɗin abinda ya shirya ,"    Yayin da ita kuwa hajiya umma baki ɗaya ta tattara hankalin ta gare shi , tana nazarin sa ," ita ta katse shirun da tambayar sa ,'     Yaya kun ka ƙarƙe da yarima ? Shin ya sanar da kai damouwar sa ? Ko kouwa ?        Ƙwarai ranki ya dade yarima ya shaida min basshi da watta damouwa da ta wucce , na rashin aboukiyar zama , inda har ya nouna ra'ayi da zai yiwu ma yana buƙatar a amra masa mataye biyu a rana gouda wanna shine ɗai guda damouwar yarima , sai kouma yace ayi albishir yana nan tafe nan da ƙarshen wata me kamawa, bayan haka yarima yana nan lafiya cikin yanayi mai kyau !    Tafeda ya ƙarasa zancen sa yana sunkui da kai da jin kunyar ƙaryar da ya gilla , wacce rashin mafita ya ja sa ga aikata ta ,"      A take fuskar hajiya umma ta yalwatu da fara'a zuciyar ta ta haskaka , har haƙoran ta suka bayyana ,"    Alhamdulillah , Madallah da kai Tafeeda yaron kirki , tashi maza ka tahi    ka sanya a fara shiri tare da gyara ga bangaren da anka gina na wagga ɗiya ƴar mutan agades , zan yi magana da mai martaba akan buƙatar da yarima ya tado da ita , amsa zai isar maka , Madallah da kai ,Madallah !        Godiya Tafeeda yayi tare da miƙewa yana barin shigifar , yana sake ganin dacewar shawarar da ya bayar na aurawa Yarima mataye ganin sa hakan ne mataki na farko na dakile sa daga sake faɗawa cikin wata musibar a gaba , domin ya ƙare nazari kaf rashin aure shine dalili na farko da har ya sa Yarima faɗawa ga zina , Yana fatan yadda ya rufa asirin mummunan labarin nan a nan gaban hajiya umma , Youssouf ma ya rufawa kan sa asiri ya bar ɗiyar chan a Nigeria kamar yadda ya faɗa masa , idan kouwa har ya ƙi jin shawarar sa babu shakka jiki magayi ,"duka da ɗanyen kara ," tsuntsun da ya jaa ruwa kuma shi ruwa kan doka , shi dai yayi iya yin sa ,"    Faɗuwa ta zo dai-dai da zama , shine abunda hajiya umma take kitsimawa cikin ran ta , ganin cewa a saukaƙe tare kuma da haɗin kan yarima auren sa da Siyama zai tabbata , kai wannan Al'amari yayi kyau gwanin daɗi , cikar gata da martaba ne ga ɗan nata ya auri mataye biyu a rana gouda , tabbas maƙiya zasu cija yatsa , girma da martaba kouwa zasu tabbata ga Yarima Youssouf ,"     Nan ta kudurce sanar da maimartaba a daren na yau da ita ke da turakar !           ***** Biyamuradi Youssouf yana barin airport inda ya raka Tafeeda gidan su Dr Hamza ya nufa , maigadi shi ya nema masa izni,   Yana shiga ya tadda prof yana karin kumallo , suka gaisa faram-faram nan ya masa umarnin ya matso su ci abincin , Babu musu ya wanke hannun sa ya matso suka fara cin abun ƙarin ,"Fankaso ne da miyar ganyen alayyahu , sai kuma danderun tsokar ƙaramar dabba , gefe guda kuma kwaɗon zogale ne da yake mahaɗin kowanne cin abinci na prof ,sai kuma green tea ,     Sosai ya nutsu ya ci abincin yana yabawa girkin maiduguri , bayan sun gama cin abincin ne prof ya gyara zama yana fuskantar Youssouf ɗin ,cikin nazari yace     Zan so ka sanar da ni takaitatcen tarihin ka da kuma halin da ka kasance a ciki bayan rabuwar ka da iyalin ka da ta sanar da mu cewa ka mutu sanadin ƴan tawayen nan na boko haram ,"      Shiru yayi yana jin yadda tausayin ta ke sake mamayar sa , Allah sarki ashe ta rufe kome , ta rufa musu asiri , ta lulluɓe laifin sa , ta gyara masa asalin ɗiyar sa a idanun jama'ar ta , idan haka ne shi kuwa zai cigaba da kare martabar ta a idanun su har abada , shi ma bazai taɓa tono laifin su da ta binne ba ,   Asali na ni mutumin niger dagga yankin ,"Malbaza Uzine," dake ƙassar Tahoua ," ni sojja ne aiki ya shiggo da ni nan nigeria har munka yi amre da itta , bayan amren mu bada jimawa ba boko haram sunka kawo hari mahaɗar mu inda sunka far mouna da yakin da yayi sanadiyyar rabouwar mu har ta kai ga tayi zaton na moutu, sun ka yi gudun hijira zouwa nan ,"   Lokacin da kuka yi aure a hannun iyayen ta ta karbi auren ta ?       Mukut ! Biyamuradi ya haɗiyi yawu , shi wannan mutumin matsayin me yake gare ta ? Zaton sa ɗan ouwa ne ga mahaifi ko mahaifiyar yarinyar ," Cikin ƙosawa yace    Mahaifi gare ta ya rassu , sai dangin ta ,"     Kayi hakuri ina maka tambayoyi ne domin mu tabbatar da gaskiyar Alaƙar ku saboda yau duniya babu gaskiya ," Mu ma ta shaida mana mahaifin ta ya rasu sanadin tarzomar boko haram , mahaifiyar ta tare da sauran dangin ta sun bata , ta zo nan mun ƙarbe ta tare da ƴar uwar ta sai kuma juna biyu tare da ita wanda ta rasu wajen haihuwar ƴar,  ɗan waje na shine ya kawo su nan bayan ya tsince su suna walagigi cikin wahalar rayuwa a bakin titi ,   Ya tsahirta , Yana duban Youssouf wanda idanun sa suka yi jaa saboda jin tausayin Yakaka da ahalin ta,    Idan har dattijon nan da ya ɗauka wani jigo ne ga yakaka , yace shi bashi da wata alaƙa da su asalima taimakon su ɗan sa yayi suka kasance ƙarƙashin inuwar su , shi kuwa ai babu dalili ɗaya da zai sa ya bar ɗiyar sa hannun su , wajibi ne ya tafi da ƴar sa , Kamar Prof ya san tunanin da Youssouf ɗin yake yi , sai yace da shi     Idan ka shirya tafiya da ƴar ka , koyaushe zaka iya zuwa ka amshe ta , tana tare ne da ƳAR UWA ga mahaifiyar ta wacce ka gan ta riƙe da ita jiya ," A hankali ya ɗago kan sa , yace zan iya ganin su ? Ƙwarai kuwa bari a ƙira su ," Cikin mintuna kaɗan falmata riƙe da baby mama ƙarƙashin jagorancin hajja mai wurya suka bayyana a falon , fuskar falmata babu walwala , saboda ƙiran da aka mata na cewa ta kawo baby mutumin jiya ya dawo ganin ta , tambayar kan ta take yi wanene wannan mutumin da yake ta zaryar ganin baby mama ,?  Ita fa sam bata ƙaunar abunda zai ratsa tsakanin ta da ƴar kome ƙanƙantar sa , Bayan ta gaishe da prof da take jin tashin muryar sa tun shigowar ta falon ,   Yace da hajja mai wurya    Ƙarbi ƴar ki miƙa ta ga mahaifin ta , mun riga dai mun mata hudhuba tare da yanka kamar yadda addini ya zartar , ƙarƙashin yaddar uwar riƙon ta kuma ƴar uwa ta jini ɗaya da muka sani tare da yarinyar kafin bayyanar ka , amma kana da ikon sauyawa ƴar ka suna !     Janye ƴar falmata tayi ta hana hajja mai wurya damar ɗaukar ta ," Waye baban baby ? Waye yace shine baban baby ? Baby ƴar mu ce ni da yakaka na , mu kaɗai muka haife ta , yanzu da babu yakaka ni ce mama , baba , yaya , kanwa , da gabaɗayan danginta , ko waye ma yace shine baban ta ƙarya yake muku wallahi ƙarya ne , ta ƙarasa zancen tana fashewa da kuka !   Turus ! Biyamuradi Youssouf yayi yana bin fuskar ta da kallo , ƙwarai ya shaida waɗannan idanuwan nata masu girma , ita ce wannan ƴar yarinyar da ta nemi yi masa faleƙe lokacin da ya fara tako kafafun sa cikin wannan gidan , biki , a watanni baya , ashe rashin sani shi yafi dare duhu , ashe ya tako har gidan da take lokacin da yake bulayin neman ta ? Allah ya raba ganawa a tsakanin su , Wani tsoro ne ya ji yana taso masa daga ƙarƙashin ran sa , tsoron kar ƙanwar ta ta san kome ? Kar ta tona asirin da shi da yakaka suka binne ,! Kar ta furta kalmar da zai shata layi tsakanin sa da mallakar ƴar sa , dan haka cikin sarƙewar harce yace ,     Du-duba kin ka ce baki shaida ni ba ?  Baki gane ni ba ?      Cikin hargagin kuka tace waye kai ?  ni ban san muryar ka ba , aina ka san mu ?  Ni da yakaka bamu da kowa a duniya kowann mu sun mutu , sai mu biyu a karshe Yakaka ma ta mutu ta bar ni tare da baby , bamu da kowa ni da baby , Baba wallahi ƙarya yake yana so ya ƙwace min baby dan Allah ku hana shi taɓa ta ,   Wani kallon yatsutsu hajja mai wurya da daman cike take da halin ƙwalafaci da rashin yardar da falmata take gwadawa kowa akan baby mama , tace    Ji min karfin hali ?? Ji min abun mamaki ƙurege da faɗa wa zomo daɗin ƙanzo , yanzu ke saboda Allah yarinyar nan un un un Falmata kike da suna ko wa ?? Yanzu ke uba zaki hanawa ɗaukar ƴar sa ?? Ina kika taɓa jin anyi haka ? Ina kika taɓa jin ɗa ya zama ɗan mace da dangin ta ita kaɗai ?? A rashin yardar taki da kowa kuma har da uban ƴar ?? Ni dalla bani ƴa na miƙata ga uban ta , har akwai martabar da ta zarta ta mahaifi ga ɗan sa , ?   Kukan da falmata ta fashe da shi wanda ya ja ƴar jaririyar ma ta tsanyara kuka shi ya sa Youssouf zabura akan kafafun sa ya miƙe ya tsaye ,     Kyale matta ɗiyar , batta ta cigaba da riƙon ta , Fatima zahra, yi shiru abun ki babu mai raba ki da ɗiyar nan , ɗiya ai taki ce , ki daina kuka kin ga ita ma kuka take ,     Lallashin ƴar ta shiga yi tana yi tana share hawayen ta , ' Duban sa ya maida kan prof da yake yawo da idanun sa a kan su, cikin ruɗani yana son fahimtar mai gaskiya a tsakanin su ," Baba Fatima ta samou watta larura ne ?   Ya furta hakan da sigar tambaya cikin son cire zargin da ya fara hangowa a idanun prof ɗin ,   Bata da wata larura bayan wacce muka gan ta da ita ta rashin gani , sai dai ko rashin ƴar uwar ta ya sa ta a ruɗani ,! Hamdala Youssouf yayi a cikin ran sa , ashe ma makauniya ce , idan haka ne kome zai zo masa da sauƙi , Babu shakka ta shiga ɗimuwa da yassa ta gaza gane ni , a bar ta kar ayi mata zancen kome har zouwa lokacin da zan dawo bayan kammaluwar aiki na ,   Toh babu damuwa Allah ya kai mu lokacin ,    Fatima ku koma ciki tunda dai kin ƙi a bashi ƴar ,   Falmata da bata saurarar zantukan su ta himmatu wurin rarrashin ɗiyar da take gaba da sauran mutanen da suke wajen a wurin ta , cimak!  ta miƙe tsaye ,  riƙe da jaririyar da take ƙoƙarin komawa baccin ta ,     Hajja mayar da ni ciki Tace ga hajja mai wurya wacce take ta faman kyeɓe baki ,    Yanzu Allah baza ki bada ƴar nan ba Baban ta ya gan ta falmata ?    Da sauri Youssouf da har lokacin bai zauna ba yace , ƙƴale mata ɗiyar nan Babaa , batta ta cigaba da riƙon ta , ita ma ɗiyar ai tata ce ,"      Ta gaban sa suka zo giftawa , yana bin su da kallon ƙwalafacin son ya ga ko ƴar fuskar ƴar ta sa,  yadda falmata ta kumburo fuska ta haɗe girar sama da ta ƙasa yaso bashi dariya ,ita a dole kar a taɓa mata ƴar ta ,   ƙwarai sai ya ji ta burge shi , yadda ta jajirce take ƙoƙarin bada kariya ga ɗiyar sa ya motso shauƙi daga ƙasan ran sa , ashe ba shi kaɗai bane yake jarumi akan ƴar ta sa , ashe ba shi kaɗai bane yake Ƙoƙarin bata kariya , ashe bayan shi ƴar sa tana da wata ƴar ƙaramar katangar da take kare da ita , da idan ta bunƙasa zata iya zama dangar dutse da babu saran da ya isa ya samu na bayan ta , madallah da ke FATIMA ZAHRA . A gurguje Youssouf yayiwa Prof sallama da zummar dawowa nan da ƙasa da kwanaki arba'in lokacin da zai kammala aikin sa , zai dawo tafiya da ƴar sa ,     Zaro damin kuɗi yayi daga Aljihun sa ya ajiye a gaban prof ,   Baba ga wannan a ƙara cikin hidimar gida madallah nagode da karamcin ku ina nan dawowa ba da jimawa ba ! Kul ,   Ɗauki kuɗin ka , bazan karba ba , hidimar fatima da jaririya zai cigaba daga aljihuna kamar yadda yake a tun farkon zuwan su har sai lokacin da riƙon su ya bar hannun na , dan haka ka ɗauki kuɗin ka , Nagode   Ganin ba fuska ya sa Youssouf ɗaukar kuɗin sa , godiya mai tarin yawa yayi masa kafin ya miƙe yana barin gidan    Cikin ran sa da addu'ar Allah ya sa har ya dawo yarinyar nan da aka ƙira da suna fatima bata ɓata masa shiri ba , sai dai yana jin bama zata iya ba saboda ganin sa yafi kowa iko da ɗiyar sa nan duniya ! ****** Abuja Cikin sati biyu duk wani shirin makaranta ya kammala ga Yakaka , inda samy baby ta zaɓar mata ,"Eyes Scholars School ,"wacce take makarantar boko da take chakuɗe da arabi tsantsa, a matsayin makarantar da take so yakaka ta dunga karatu , Duk da cewa Alhaji Gali attajiri ne kuma fitatcen ɗan kwangila amma sai da aka samu tsaiko gurin ɗaukar yakaka a makarantar , domin a cewar hukumar makarantar yakaka bata chanchanta da shiga ajin gaba da primary ba bayan interview ɗin da aka mata kamar yadda samy baby ta so a sanya ta , hukumar makarantar ta tabbatar musu da cewa ko ɗaliban su ƴan primary school sun wuce yakaka a matakin karatu , Bayan kai kawo da Alhaji Gali da shi ke ɗauke da nawin kome na dangane da karatun yakaka , ya dunga yi Kuɗi da Alfarma suka yi aikin su inda hukumar makaranta ta amince da shigowar yakaka cikin jerin ɗaliban su ƴan matakin ajin farko na secondry school jss1 , tare da sharaɗin Alhaji Gali zai ɗauki mai yiwa yakaka ,"extra lesson",koyarwa na mussaman daga cikin malaman su na makarantar da kuma zai dunga biyan malamar a duk wata , domin a cewar su chakuɗa irin yakaka da bata san kome ba tare da sauran ɗaliban su zai iya kawo naƙasu ga karatun sauran ɗaliban su da suke aji guda da ita wanda a ƙarshe zai tado da ƙorafi daga iyayen yaran da zai iya kaiwa ga duƙushe tasirin ingancin makaranta a idanun jama'a , Ba tare da ƙorafin kome ba Alhaji Gali ya amincewa sharaɗin su , ganin sa ai duk abunda yayiwa samy baby bai faɗi ba , tana biyan sa dan haka bashi da asara , Nan take ya lale ya biya kuɗin malamar da zata dunga yin extra lesson ɗin inda aka zaɓar mata wata yarinyar mace da ashekaru zata haifi yakakar , tana tsakanin shekaru 36-38 , malama maryam ita ke ɗaukar su yakaka fannin I.R.K , ( Isalamic Religion knowledge )  abunda kuwa ya sa hukumar makaranta ta zaɓe ta shine domin zamantowar ta jajirtatciyar malama da ta kware a harkar koyarwa , duk da cewa fannin addini take koyarwa amma sun san zata iya koyar da yakaka English da Arabic sosai ta yadda gaba zata fara gane karatu da kan ta , bugu da ƙari gani da suka yi location ɗin gidan ta da na su yakaka duk ɗaya ne , dan haka suka ɗora mata wannan nawin , Babu musu malama maryam ta ƙarbi form ta cike a matsayin ta na malamar da zata dunga extra lesson na musamman ga sabuwar ɗaliba yakaka , ranta cike taf da farin cikin samun wannan damar na amsar wani ƙarin kuɗi akan albashin ta na kowanne wata wanda kusan da shi rayuwar su ita da ƴaƴan ta da mijin ta suka dogara , zuciyar ta cike da burin zage ƙwanji ta koyar da yakaka da dukkanin iyawar ta har sai watarana anyi mamaki , . Ga bangaren yakaka bata jin kowanne  irin yanayi dangane da sabuwar rayuwar ta na jin daɗi ko akasin sa , iyaka ta san har zuwa yanzu da take samun wajen sati uku a sabuwar rayuwar ta , kewa tare da so gami da tausayin rayukan nan biyu da ta bari a bayan ta yana nuƙurƙusar zuciyar ta tare da yiwa walwalar ta kisan mummike , Ko yaushe kewar falmata ta dame ta takan zauna tayi kuka iya kuka , tana son sanin a wanne hali suke ciki ita da ƴar jaririyar da ta bari ? Tana son jin tashin muryar falmata , Sai dai a ɗan tsukin zaman da ta fara yi a gidan samy baby da irin mutanen da take gani a gidan tare da saurarar wasu daga cikin hirarrakin su da fiye da rabin sa ba ganewa take ba , ya sa ta sake kafa naci akan neman ilmi ya kuma sa ta fahimci shi ilmin ashe muhimmancin sa ya kai sai ya wadata ga mutum sannan mutum yake samun cigaba da kaiwa ga wani matsayi a rayuwa , dan haka ta kuɗurta cikin ran ta a yanzu komawar ta ga su falmata bai da amfani , zata tsaya ne ta nemi ilmi iya yin ta , tunda dama ta samu gare ta ,  ta yadda ita ma zata tsaya da kafafun ta , ta koma rayuwar ta ta baya ta gyaro kuskuren ta , ta ɗauke ƙanwar ta da ƴar ta , su ma ta tsaya musu suyi karatu su samu ilmi , bata tunanin akwai azal , bata tunanin lokacin ba a hannun ta yake ba , bata tunanin shi lokaci juyawa yake yana wucewa cikin kowacce daƙiƙa da idan kuma har ya wuce baya dawowa , shin ko lokaci zai jira yakaka har zuwa cikar burin ta kome yana nan yadda yake kamar yadda ta tsara shi take kuma buri ??? Duk yadda yakaka tayi zaton samun ilmi na da sauki ta tadda abun ba haka nan yake ba domin tun ranar da ta sanya kafafun ta cikin makarantar da awanni kaɗan da suka wuce daga ta tuno da kusantowar ta ga fara zuwa makaranta neman ilmi ji take farinciki na mata lulluɓi , da har take sakin murmushi akai akai , Labarin ya sha banban lokacin da yakaka ta sanya ƙafafun ta cikin ajin da aka mata jagora tare da bata tabbacin nan ne ajin karatun ta , Tayi zaton zata tadda ƴan mata sa'o'in ta ne a ajin a matsayin abokan karatun ta , sai ta tarar da yara ƙanana da manyan cikin su ma Falmata zata iya girme musu , Jiki a sanyaye ta bi bayan mai mata jagora inda ya kai ta chan ƙarshen ajin ya nuna mata wajen zama , Zama tayi tana satar kallon yaran da kusan su dukkanin su suka waigo suna bin su da ido ,,alamun mamaki ɗauke akan fuskokin su har wasu daga ciki na magana da junan su ƙus-ƙus Hankalin ta bai sake tashi ba sai da ta ga malami ya shigo yayi koyarwar sa ya gama , bata kai ga fahimtar ko kalma guda ba saboda bata jin yaren da yayi magana da shi , cikin rashin sanin ta bayan darasin da malamin integrated science ɗin ya koyar da su har ,"class work/aikin cikin aji ,"ya bayar yana jiran su kammala ya bi ya duba   , Ɗaya bayan ɗaya ya dunga bin ɗalibai yana duba class work ɗin da ya basu , ya yabawa wasu , wasu kuma ya gargaɗe su , duk dai cikin yaren da yakaka ba fahimtar sa take ba , har ya zo kan ta ,   Wani kallon gargaɗi yake jefa mata Hey what are you doing here? Go back to your class  now ," Ƙifin-ƙifin da ido yakaka take yi tana kallon sa , tare da wasa da bakin ɗan madaidaicin hijabin ta, I say Go back to your class,!   Ya daka mata tsawar da ta firgita ta Dariyar da mafi yawan yaran ajin suka kwashe da ita shi ya sa malamin mayar da hankalin sa gare su , Hey what's wrong with you class ? Uncle she is our classmate , she's a new comer,  Wasu yara kusan su hudu suka haɗa baki wajen faɗi , suna cigaba da dilliƙar dariyar da tun shigowar yakaka suke son yin ta ,   Ya buɗe baki da nufin sake yin wata maganar shigowar malama Maryam ta katse shi , Ɗalibai suka miƙe domin gaishe ta ta dakatar da su ,suka koma suka zauna  tana jefa musu tambaya cikin harshen larabci tace   Aina huwa ɗalib jadid Yakaka Gali ? Da hannun su suka yi mata nuni da inda yakaka take zaune ta sunkui da kai idanun ta taf ƙwalla , tana jin yadda idanun malamin nan ke yawo akan ta da kallo mai ɗauke da ƙasƙanci , Ɗan takaitatcen bayani malama maryam tayiwa malamin nan akan yakaka a ƙarshe ta nemi alfarmar tana so tayi magana da yakaka a wajen class , Ya bata izni yana shaida mata shi ya gama da ajin ma , lokacin sa ya fita , sai na malamin darasin gaba , Da hausa malama maryam tayiwa yakaka tausasan kalamai tare da gabatar mata da kan ta a matsayin malamar ta da zata dunga koyar da ita inda ta nemi da ta jajirce akan duk wani ƙalubale da zata fuskanta a yayin neman ilmi , ta kuma dage ta buɗe kwakwalwar ta ya zama tana maida hankali tana koyon duk abunda ake koyar da ita  , har ma tayi mata albishir a gaba idan ta dage ta iya karatu za'a mata chanjin aji zuwa na manya sa'annin ta , a ƙarshe kuma ta gargaɗe ta akan ko kusa kar ta bada ƙofar da yaran nan zasu raina ta , ta tsayar da karfe 7am na safe zuwa 8am a matsayin lokacin da zata dunga koyar da yakaka darussan da suke cikin yaren English , karfe 4pm zuwa 5pm kuma ta koyar da ita Arabic da littatafan addini , Godiya mai tarin yawa yakaka tayi mata tana share ƙwallar idon ta da hannuwan ta biyu , Kafin ta juya ta koma cikin ajin ƙarƙashin umarnin umarnin malama maryam ! Cikin kwanakin da suka biyo baya yakaka ta kafa naci ta ƙarfi da yaji so take ta ga tayi ilmi ," bata da wani lokaci sai na karatu ta tattara duk wasu al'amuran da suka shafi rayuwar ta na baya ajiye shi a waje guda cikin zuciya ta ta killace su gefe , da gaske so take ta yaƙi jahilci , so take ta ci gajiyar ilmi so take ta goge kalmar wawanci da aka mata laƙabi da shi , so take lokaci yayi saurin juyawa wanda zai zo mata da sauyi daga JAHILA ZUWA MALAMA . Gidan malama Maryam bayan layin gidan samy baby ne , ɗan madaidaicin  gida ne inda suke rayuwa ita da mijin ta da ƴaƴan su uku , babbar ƴar ta lubna zasu iya zuwa sa'anni da yakaka , sai maza biyu faruq da sadiq , a halin yanzu Lubna tana ss2 , faruq yana ss1 sai sadiq da yake jss3 , mahaifinsu ƙaramin ma'aikaci ne da yake aiki da wani company ," Rayuwar gidan Malama maryam abun sha'awa ce duba da yadda suke masu ƙaramin ƙarfi amma rayuwar su cike take da wadatar zuci , soyayya da shaƙuwa gami da tausayin juna a tsakanin iyayen da ƴaƴan su ya yawaita , da hakan ya zama abu mafi muhimmanci da ya haifar da ingantatciyar tarbiyya a wajen ƴaƴan su , tare da taimakon tsayayyar uwa da suka samu , malama maryam mace ce wacce ilmin addini ya wadace ta , take kuma aiki da shi,  a yanzu matakin karatun ta degree ne a fanni Arabic And Islamic Studies , sai dai mai fadadawa tare da zurfafawa cikin neman ilmi ce musamman ma na addini,  a bangaren bokon ma ba baya bace , Yanayin ɗabi'un ta su ke sanya take birge duk wasu mutanen da suka mu'amalance ta , komen ta cikin tsari da nutsuwa take yin sa , bayan wadatatciyar tsaftar da ta bayyana kan ta agare ta a duk inda ta kasance , A tun ganin farko da Malama Maryam tayiwa Yakaka yadda ta tarar yara na yi mata dariya , ta ji tausayin yarinyar ya tsirga mata , ta san babu shakka wani shamaƙi mai girma ne ya tauye yarinyar ya hana ta samun ilmi akan kari , dan haka ta ƙudiri aniyar jan ta a jiki , ta yadda zata tunga taimaka mata tare da ƙarfafa mata akan harkar karatu ,  Ganin suna kaiwa har kusan magariba kafin su dawo gida idan ta tsaya yiwa yakaka lesson saboda nisan dake tsakanin makarantar da unguwar su , yasa ta cewa yakaka su dunga komawa gida tare idan kowaccen su ta je gida tayi sallah ta ci abinci , sai yakaka ta zo har gidan ta suyi lesson ɗin , wanda lokacin da take ɗauka tana yi mata lesson ɗin ma ya zarce awa ɗayan da makarantar ta sharɗanta mata , Sannu sannu saboda nacin karatu irin na yakaka da kuma samun fuska da tayi wajen malama maryam da take kira ,"anty," wacce ta sake mata sosai babu tsangwama ko kyara a yayin da take koyar da ita , ya sa har ranakun da babu makaranta ma yakaka zuwa take su ɗauki lokaci ana mata lesson ko na arabi ko na boko , wanda malama maryam ta lura yakakar tafi kafa naci akan na bokon tamkar dai tana da wani lulluɓaɓɓen burin da take son cikawa ta hanyar karatun bokon , babu laifi ƙwaƙwalwar yakaka tana da saurin fahimta hakan ya sa take jin daɗin koyar da ita , A hankali sabo ya fara shiga tsakanin yakaka da lubna wacce take yarinya mai tsananin wayo , hankali da manyance , cikin abunda bai fi sati uku ba da fara zuwan yakaka gidan su ƙawance ya ƙullu tsakanin su kasancewar halin su na nacin karatu da ya zo ɗaya , saboda lubna mai naci da ƙwazon karatu ce duk kuwa da cewa makaranta mai sauƙin kuɗi suke karatu ita da ƙannen ta , amma saboda kaifin ƙwaƙwalwar su , da kuma tsayuwar iyayen su akan fannin karatun su ya sa ko yaran da suke karatu a shararrun makarantu kuɗi baza su fi su ilmi ba ," Nacin karatu biyu ta haɗu dan haka bayan lesson ɗin malama maryam , lubna ma ta na koyawa yakaka wasu abubuwan da suke ma sunfi matakin karatun ta , a cewar lubna lokacin da yakakar zata kai matakin ta riga ta koya baza ta ji wahalar karatu ba , A wani yammaci lubna da yakakar suna zaune kan ƴar darduma a tsakar gida bayan lubna ta gama koya mata karatu , suna ƴar hirar su kafin malama maryam ta gama ƴan aikace-aikacen da take yi a ɗakin baban su ,    Lubna ta dubi yakaka wacce ta duƙufa tana kwafar rubutu daga jikin textbook ɗin ta ,      Yakaka ku ƴan wanne gari ne ? Naga zane a fuskar ki , kuma hausar ki ma wata iri ?     Ba tare da ta ɗago ba tace   Ni ƴar maiduguri ce !    Su maman ku da ƴan uwan ku duk suna maiduguri ne , ? Kin ce nan da antyn ki kike zaune ,    Tsam yakaka tayi ta bar rubutun da take ,"    Ganin shirun ta ya ɗauki lokaci ya sa malama maryam fitowa daga ɗaki da duk hirarrakin nasu daman a kunnen ta yake ,    Lubna tashi maza ki ɗora girki , yakaka kawo textbooks ɗin ki mu fara  karatu ,     Babu kuzari tare da walwala a gare ta suka yi karatun suka gama da bata wani fahimta ba ko kusa , da malama maryam ta lura da kyau ma sai ta ga taruwar hawaye a gurbin idon yakakar lokacin da suke yin sallama zata tafi gida , bata ko jira rakiyar lubna da take raka ta kofar gida ba , tayi tafiyar ta , Tana fita malama maryam ta ƙira lubna ta zaunar da ita tayi mata faɗa sosai akan bincikar mutum game da abunda ya shafi rayuwar sa kai tsaye ba tare da shi wannan mutumin shi yayi ra'ayin kan sa , ya bata labari ba,    Nan tayi ta ba wa mamar ta hakuri tace baza ta sake ba, malama maryam tace ita ba ita zata bawa hakuri ba , yakaka zata ba wa ,"   nan tayi alƙawarin gobe idan yakaka ta zo zata bata haƙuri ,    Tun a hanya yakaka take kuka shaɓe shaɓe da hawaye har ta ƙarasa gida , tana shiga kai tsaye ta wuce samy baby tare da ƙawayen ta da suke baje a falo suna hirar su , kowacce ta bararraje kai ba ɗankwali sai tilin izgar roba da aka yi musu kitso da shi a ka ,   Chan lungun gado ta samu ta Zauna gami da haɗa kan ta da jikin gadon ta fashe da kuka me fidda sauti , kukan tausayin rayuwar da ta bari a baya , kukan ƙewa da famuwar ciwon da ke binne a ƙasan ran ta , kukan tunowa da iyayen ta , ƴan uwan ta ,garin ta , asalin ta , kukan rashin kowa na ta da tayi ,      Yaks kukan me kike haka ? Cewa nake yanzu lokacin kuka ya wuce a wajen ki ? Ashe har yanzu baki san cewa kuka baya maganin kome ba ? Baya sawa bare ya hana ?    Ko kuwa wani abun malamar ta ki tayi miki yanzu na je na ci mata mutunci ? Ki min magana mana ?     Idanun ta jazur ta ɗago kai , anty samy na tuno da su mama , baba , falmata da baby mama , bani da kowa anty samy , ni bani da kowa !    Da wata irin murya mai ɗauke da tausayi , samy baby tace ,     Kina da ni yaks , ni zan cike miki gurbin su , har zuwa lokacin da zaki koma musu ,     Wasu sabbin hawaye ne suka zubowa yakaka ,    Falmata fa ? Waye zai zama madadi na a wajen ta ? Falmata bata da kowa ita ma idan gidan su rahima suka gaji suka kore ta ina zata je ita da baby mama ? Anty samy ina son komawa na zo da su ,!        Babu wanda zai kore su a gidan su doctor , doctor da baban sa mutanen kirki ne , ki kwantar da hankalin ki , ba yanzu bane lokacin da ya kamata ki ɗauki nawin su lokacin na nan zuwa kin ji ko ?    Naji anty samy , Yauwa ko ke fa ? Yakaka matar Yarima ta furta hakan tana juyawa ga barin ɗakin ,   Da wani irin kallo yakaka ta bita ,     Yarima   Ta maimaita ! **** Kwanakin kammaluwar aikin Biyamuradi Youssouf Tare da komawa ƙasar sa suna sake kusantowa , aiki yana sake zafafa a gare su , inda cikin ƙasa da wata ɗaya aka samu asarar fiye da sojoji hamsin cikin rundunar sa , wanda hakan ko kusa ba abu ne mai dadi ba wajen su da ma gwamnatin ƙasar su baki ɗaya , duk kuwa da cewa aikin soja daman ya gaji haka , sadauƙarwa ne a bakin rayukan su , Dan haka duk yadda ya so ya samu damar zuwa sake ganin ɗiyar sa abu ya gagara dole ya haƙure har zuwa nan da kwanaki goma da wa'adin su yake ƙarewa , Baby mama sai girma take tana daɗa wayo , har ta wuce kwanaki arba'in tana neman cika watanni biyu , kome ƙin ka da jariri idan ka ga baby mama sai ta burge ka , ka ji kana son ɗaukar ta , idan kuwa ka ɗauke ta ji zaka yi ina ma a baka ita , ina ma ƴar ka ce ? Yarinya ce mai tsananin ruwan kyau bayan kyaun kan sa da take da shi , ƴar bul-bul da ita fara tas gwanin sha'awa madarar jariran da ake bata ta karbe ta ba'a ce jaririyar da ta barranta da shan nonon uwa bace ba , Bugu da ƙari kulawa da lelen da Falmata take yi mata domin duk da kasancewar falmata makauniya , tsafta yana daga halittar ta ce , dan haka ko yaya ta ji wani yanayi da bai gamsar da ita ba a tare da baby mama , take zata tuɓe ta ta goge mata jiki da wiper , ko ruwan ɗumi da tawul ta sauya mata diaper da kaya , bayan wanka sau biyu da hajja mai wurya take mata safe da yamma ," dan haka koyaushe baby mama cikin ƙamshi take da wankakkun kaya tsaf-tsaf , So da ƙaunar baby mama a bayan kowacce daƙiƙa sake ninkuwa yake cikin ran falmata , ta ɗauki duk wani so ƙauna da tausayi na duk wasu mutanen da ta taɓa so a rayuwar ta rashin su ya sa ta juye su akan ƴar jaririyar , tamkar ran ta aka taɓa haka take ji idan tace 'uhun' da sautin kuka , bata taɓa gajiyawa da hidimar baby mama , ta kan manta da yunwar cikin ta ko ƙishirwa idan ta shagaltu cikin tarairayar ta , son baby mama haɗe yake da bugun zuciyar falmata ! Waƙoƙi iri iri take rera mata da ƴar daddaɗar muryar ta cikin yaren su , sai kuwa ƴar jaririyar tayi luf , ƙulus a kwance tana kallon fuskar falmata da tunda ta fara kallon abubuwa ta himmantu gurin tsare fuskar falmatan da idanun ta a duk lokacin da take farke , ga alama bada jimawa ba zata haddace kamannin ta tare da ɗaukar yanayin ɗumin jikin ta , ta kuma gane warin jikin uwar goyon ta da ta buɗi ido tun ranar farko ta gan ta a matsayin UWA a gare ta ," ****** Duk abunda aka sanyawa lokaci aka zana iyakar sa to fa babu shakka zai zo ya wuce tamkar da ɗai ba'a taɓa fara farkon sa ba , Yau shabiyu ga watan goma sha biyu ita tazo dai-dai da ranar kammaluwar aikin tawagar rundunar sojojin niger da suka kawo tallafi wurin yakar ƴan tawayen Boko Haram zuwa cikin yankin nigeria ta kan boda inda yankunan biyu suka haɗu na niger da nigeria , ƙarƙashin jagorancin Colonel Youssouf Abdul-Azizou Baskore , a kuma yau gwamnatin ƙasar su ta bada umarnin su fara janyewa daga filin daga inda waɗanda aka turo su maye gurbin su zasu samu isowa bakin dagar a yau , '  dan haka baki ɗayan sojojin gurin idan ka dubi fuskokin su a yalwace suke da fara'a , inda dayawa daga cikin su suke ta ihu da wasanni a tsakiyar dajin domin bayyana murnar su a fili kan komawar da zasu yi ƙasar su cikin dangi da iyalan su , bayan kwashe fiye da tsawan watanni goma sha biyu da suka yi cikin daji , Colonel Youssouf ya bi jerin ƴan uwan sa soji wajen bayyana farin cikin sa bisa ga wannan nasarar da suka samu na tsallake hare-haren ƴan tawayen boko haram ɗin da suka sha far musu , da kuma nasarorin da suka samu wajen fatattakar ƴan tawayen boko haram ɗin ta hanyar kashe wasu tare da kama wasu da dama , hakan a gare su babban nasara ne da dukkanin su suke sanya samun ƙarin girman matsayi daga gwamnatin ƙasar su , Gefe guda kuma zuciyar sa cike taf da murnar sake ganin ɗiyar sa da zai yi a yau , sosai ya zaƙu yake kuma ɗora idanun sa akan fuskar ta , dan haka duk wani abunda yake cikin ƙuzari da karsashi yake yin sa ,  Sha biyun rana tawagar sojin da zasu karbi aiki suka iso ba tare da ɗaukar dogon lokaci ba bayan musayar gaisuwa da wasu bayanai na sirri irin na tsaro da ya shiga tsakanin manyan sojojin gurin da zasu tafi da sabbin da zasu maye gurbin su , Motocin da suka kawo sabbin sojin suka fara juyawa da tawagar masu komawa inda zasu ajiye su a babban  barikin garin maiduguri zuwa gobe da zasu wuce ƙasar su ta jirgi da zai tashi ta abuja ! Biyamuradi Youssouf bai jira rana tayi sanyi ba , da isar su barikin maiduguri , wanka kawai yayi ya sauya kayan sa daga uniform ɗin soji , Ɗaya daga cikin direbobin su ya ja sa zuwa unguwar da ƴar sa take , Ƙarfe ɗaya na rana ta gota suka isa gidan nan ya tadda prof tare da wasu baƙin sa ,dan haka ya jira su har suka gama ganawa sannan ya shiga falon , Bayan gaisuwa da suka yi prof bai bari ya ɗora kome ba yace bari suyi sallah su ci abinci , Bayan sun ɗan taɓa abincin da ba sosai Biyamuradi Youssouf ya ci ba , Prof ya tattara hankalin sa ga Youssouf yana saurarar sa inda yake sanar da shi ,    Yana so gobe ya zo ya ɗauki ɗiyar sa saboda a goben yake son komawa ƙasar su domin aikin sa ya kammala ,' Shiru prof yayi yana ɗan nazari yayin da zuciyar yarima ta cika taf da taraddadi tare da fatan kar wata matsala ta taso domin zuwa yanzu ya gama tsara kome game da makomar rikon ƴar sa a tare da shi , ya gama tsara inda zai kai ta tayi rayuwa irin wacce yake so ƙarƙashin inuwar kulawar sa da kuma kariyar sa , dan haka baya jin akwai wani abunda ya isa ya hana shi ɗauke ɗiyar sa daga hannun waɗannan mutanen da bai kai ga sanin su ba basu kuma da kowacce irin alaƙa da shi da har zai iya barin jinin sa tare da su , ya shirya tsaf ko ta tsiya ko ta arziki zai tafi da ƴar sa ! Gyaran murya prof yayi kafin ya ɗora da cewa ,     Ɗa na mai zai hana idan har ka amince ka bar jaririyar nan a hannun ƴar uwar mahaifiyar ta har zuwa lokacin da ta ɗan tasa tayi wayo shekaru biyu zuwa uku sai ka dawo ka ɗau ƴar ka , baka ganin yanzu idan aka raba yarinyar nan ƙanwa ga mahaifiyar ƴar , zata shiga damuwa me tarin yawa ganin cewa har zuwa yanzu ba ta kai ga gyagijewa daga ruɗanin da mutuwar yayar ta ya jaza mata ba ,bugu da ƙari bata da kowa nata a halin yanzu sai ita wannan ƴar ta ka , ka duba magana ta da kyau ,    Ya ƙarasa zancen da bada zaɓi ga Biyamuradi , Ba domin tun ganin farko da Youssouf ɗin ya yiwa prof ɗin ya riga ya cika masa ido da ƙwarjinin sa tare da cikar kamalar sa ba , sannan halin dattaku da mutuntaka da ya dunga nuna masa a kowacce haɗuwar su , mafi muhimmanci kula da rayuwar ƴar sa da yayi na wani lokaci , bayan haka da babu abunda zai hana ya kartawa prof rashin mutunci , ya kuma gwada ƙarfin ikon sa na soja , sannan da ƙafafar su ta sarakai da koyaushe abunda suka so shi ake mu su ba'a musa mu su , ya ɗauke ƴar sa yayi tafiyar sa , to amma girma prof nada yawa a idanun sa dan haka ya sassauta murya tare da saita nutsuwar sa yace    Baba nan ba kassa ta ba , sannan ni kuma ai ma'aikaci ne , idan na tafi na bar ɗiya ta nan hankali na basshi kwanciya , chan inda zan tahi da ita nan ai shi tushe da assalin ta , kayi haƙuri baba zan tahi da ɗiya ta na ɗau Alƙawarin zan wanzu ina kawo ta lokaci zuwou lokkaci ta ga innon ta da yardar Allah , Shiru prof yayi yana jin tausayin falmata na kawo masa , bashi da wani ƙarfin iko akan yaran , bai haɗa kome da su ba idan banda taimakon su da ya biyo ta hannun sa dan haka shi baya da ƙarfin hanawa Biyamuradi ɗiyar sa ,     Toh bari a ƙira ita uwar riƙon ƴar ta ji daga bakin ka , kafin gobe da zaka dawo ɗaukar ƴar , Rahima ce ta rako falmata a yau da kallo ɗaya za'a mata a gane gaf take da ɓarkewa da kuka saboda ƙiran da aka mata ta kawo baby mama    Daga gefe ta gurfana bayan ta gaishe da prof , tayi shiru , Fatima ga baban jaririya nan ya sake dawowa yau , miƙa masa ƴar sa ya gan ta ,     shiru tayi bata ce ƙala ba     A hankali Rahima ta zare baby mama daga hannun ta wacce take ta wasa da hannuwan ta idanun ta tar a buɗe , shirye take tsaf cikin jar riga ta jarirai mai haɗe da wondo da safa , kan ta lulluɓe da farar hular sanyi mai ratsin ado da fulawoyi jajaye , Hannun Youssouf har rawa yake lokacin da yake ƙarbar yar jaririyar , yana ƙarbar ta ya zarce da ita zuwa fuskar sa inda ya sumbanci kumatun ta zuwa goshin ta , bakin sa ɗauke da addu'o'i ya kama wannan ya Sake waccen , Farin cikin sa ya yawaita da har ya gaza boyuwa ya bayyana akan fuskar sa dake ɗauke da murmushi mai bayyana haƙora , maida ita ƙirjin sa yayi ya rungume ta rungumar da ke bayyana tsantsar so da ƙaunar da yake mata , ji yake kamar ya buɗe cikin ƙirjin sa ya ɓoye ta ,    Da dariya akan fuskar sa ya ɗago cikin cewa     Ɗiya ta girma sossai , hala wanni sinadarin ƙara wa jarirai girma da lafiya kuke bata ?  Madallah Madallah da ku , "      Ɗan murmushi prof yayi , kafin ya maida ganin sa kan falmata wacce ta ƙagu a miƙo mata baby mama suyi tafiyar su ,   Fatima kina ji na ko ? Ina ji Baba   Ta amsa da ladabi cikin muryar ta , Baban jaririyar nan ne ya zo yau yake shaida mana ya gama aikin sa da ya kawo shi nigeria nan ƙasar mu , dan haka gobe yake son komawa tare da ƴar sa , a shiryawa jaririya kayan ta kafin gobe , Tamkar kunnen ta ya toshe haka ta ji dumm , cikin kan ta , tana jin yadda kalmar a haɗa kayan baby mama za'a tafi da ita gobe yana bin duk wata gaɓɓa mai kuzari a jikin ta yana kassarawa ,   wanne azzalumi ne yake neman ta ƙarfi da yaji sai ya raba ta da jinin ta ɗaya tal da ta rage mata a duniya , ? Da wani nisasshen yanayi cikin muryar ta ta ɗago kan ta tana saita idanun ta inda ta ji tashin muryar youssouf ɗin a ɗazu tace Wanene kai ? Me muka maka kake son raba mu ? Aina kasan yakaka na ?meyasa kake ƙarya ?   Shiru tayi tana jin yadda fitar numfashin ta ke sauyawa kafin ta ce cikin ƙarajin kukan da ya taho mata , ƙarya kake baby mama bata da BABA kai ba baban ta bane , yakaka ita kaɗai ta haifi baby mama , ina kake lokacin da yakaka take rashin lafiya akan cikin baby mama ? Ina kake lokacin da yakaka take shan wahala alhali baby mama tana cikin ta ? Aina kake lokacin da Yakaka na ta mutu sanadin haihuwar baby mama ??  Ƙarya kake kai mugu ne , ba kai bane baban baby kana so ne ka gudu da ita ,    rarrafawa tayi inda ta ji sautin baba prof yana ƙoƙarin son katse mata maganganun ta , Illahirin jikin ta rawa yake lokacin da ta dangana da jikin kujerar da yake zaune ,    ba-ba-Baba bani da kowa sai baby yakaka dan Allah kar ku bari ya raba ni da ita wallahi ƙarya yake yi maka , Baba ni miskiniya ce dan Allah kar ka bari ya zalunce mu ni da baby yakaka dan Allah Baba ,!   Wani irin yanayi me wuyar fassara prof ya tsinci kan sa a ciki ƙwarai da yana da iko da yau ya hana youssouf ɗaukar jaririyar nan ya bar ta a hannun yarinyar nan , " Idon sa ya sauke akan Youssouf ɗin wanda kan sa yake sunkuye yana kallon fuskar ƴar sa ,tamkar bai san da bulayin da Falmata ke yi ba, sam baya so tausayin falmata da ya fara tsirga masa ya sanya shi barin ƴar da Allah ya jarabbe shi akan ta  hannun mutanen da ba shi da tabbacin zasu iya riƙon ta har tsawon rayuwar ta ba , kar watarana ta walakanta ko ta sha wuyar rayuwa , ƴar sa mace ce ƙwarai tana buƙatar uba a halin tafiyar rayuwar ta nan duniya , shi ya barranta daga samari irin sa waɗanda zasu samu haihuwa ta haramtatciyar hanya su ƙarawa kan su zunubi ta hanyar yin watsi da abunda suka haifa ko ma su kashe baki ɗaya , yana so ya ubangiji ya yafe masa akan zunubin da yayi ma ta hanyar samar da ita baya fatan shaiɗan ya sake jaan sa ya aikata wani zunubin da yafi wanda ya aikata a baya muni , Mayar da ganin sa prof yayi ga Falmata cikin sigar rarrashi yace fatima ki daina cewa jaririyar nan bata da Baba , alhalin ga baban ta nan a zaune  yana jin ki babu kyau haka , kiyi haƙuri ki bari ya tafi da ƴar sa yayi alƙawarin zai dunga kawo ta nan gidan gurin ki kin ji ko ? sai lokacin Youssouf ya ɗago kan sa ya dube ta ,    Ƙwarai nayi alƙawari ƙanwa ta,  zan dunga kawo ta zouwa gare ki har girman ta , ke ai har abada uwa kike a gare ta , Zumbur ta miƙe tsaye , cikin takun da kafafun ta ke harɗewa ta nufi inda take jin tashin muryar sa ,   Hannun ta duka biyu ta miƙa da zummar riƙe sa yayi saurin kaucewa yana sake boye baby mama cikin ƙirjin sa ,     Gefen rigar sa tayi wa wani ƙaƙƙarfan riƙo ba da wasa ba , Cewa take   Dan Allah ! Dan Allah ka ji tausayi na ka bar min baby , Dan Allah kar ka raba ni da ita , zan mutu idan ka ɗauke ta , dan Allah .....        Numfashin ta ne ya fara tsarƙewa dai-dai da ƙarasowar Rahima wacce prof ya yiwa umarni da ta janye Falmata  , hawayen tausayin Falmatan suna zarya a kumatun ta , Luuuu ta tafi baya ta faɗi bisa jikin rahima suka ƙarasa bajewa a ƙasa tare babu alamun numfashi ga Falmata ,   subahannalahi innalillahi wa inna ilaihi raji'oon sune kalmomin da prof ke jerowa    Rahima ƙira direba maza a kai ta asibiti ,    Da sauri Youssouf ya waigo tare da sunkuyowa kan falmata ya tabbatar dai bata numfashi nan take ya sanya hannu a aljihun sa yana ƙiran direban sa , lokaci guda fuskar sa na bayyana ruɗanin da yake ciki yake cewa    Daman bata da lafiya ne Baba ??   Prof bai amsa masa ba , Direban youssouf shi ya fara shigowa dan haka rahima ta fara ƙoƙarin ɗaga falmata sai dai ta kasa , saboda tayi mata nawi , Baby mama Youssouf ya miƙawa Rahima ,    Lokaci guda ya sanya hannunwan sa biyu ya ɗaga falmata wacce take sume  ya fice da ita wajen motar su , direban sa ya buɗe gidan baya ya shimfiɗe ta , Ya karɓi baby mama daga hannun rahima tare da yi mata umarnin ta shiga su tafi ta gwada musu asibiti mafi kusa da zasu kai falmata , tafiyar mintoci biyar suka isa wani asibiti mai zaman kan sa , inda nan take likitoci suka rufu akan falmata suna ƙoƙarin dawo da numfashin ta dai-dai , Hankalin Youssouf baki ɗaya a tashe yake ya kasa zaune ya kasa tsaye , sai zirga zirga yake tsakanin kofar ɗakin da Falmata take yana rungume da baby mama , tsoron sa ɗaya kar yarinyar nan ta mutu a sanadin raba ta da yace zai yi da ƴar sa , idan haka ta faru bai san inda damuwar sa zata kai ba , "  ko kusa bai san haka take ƙaunar ƴar sa ba , ya kasa kintata yawan ƙaunar da ke tsakanin ta da yayar ta wanda yake da tabbacin son da take mata ne ya shafi ƴar ta , idan kuwa haka ne lalle falmata abar a tausayawa ce , ƙwarai ya kamata yayi adalci ya kuma duba anya idan ya raba ƴar sa da ita ya kyauta kuwa ?? Anya bai so kan sa dayawa ba kuwa ? mintoci arba'in da shigar da ita ɗakin suka fara jiyo gunjin kukan ta , tana surutai ,     Da sauri Biyamuradi youssouf ya ƙarasa gaban ɗakin dai-dai da fitowar babban likitan , Mun samu numfashin ta ya dai-daita kamar yadda muke zaton kun sani tana da asthma , toh ta samu attack ne , yakamata a dunga kiyayewa da duk wani abu da zai iya kawo mata wahalar numfashi , yanzu ku shiga akwai wanda take son gani a tsakanin ku , nan da ɗan wani lokaci kaɗan ma zaku iya tafiya gida ko awa ɗaya haka nan gaba ! Biyamuradi youssouf ne a gaba sai Rahima biye da shi , suna shiga rahima ta ƙarasa ta rike hannun ta , tace ga ita    Ki daina kuka haka fatima , ai ga baby nan ba'a tafi da ita ko ina ba , Tana ina ??    Tace tana lalube da hannuwan ta biyu idanun ta har sun rine tsabar kuka , A hankali biyamuradi youssouf ya tako zuwa gaban gadon ya ɗora mata baby mama a cinyar ta tare da cewa    Ungo ta ! karɓe ta fatima daina kuka , ke ai uwa ce a gare ta ,   Chak ta ɗauke ta ta rungume ta tana ajiyar zuci tare da shafa bayan baby mama tana ɗan bubbugawa , Juyawa yayi ya fita yana jin yadda tsananin tausayin ta yake ratsa kowanne saƙo da lungu na zuciyar sa yana samun mazauni , ji yake kome yana neman kunce masa , tausayin ta kuma yana neman yin tasiri akan sa , mafita yake nema , Zuwa yayi ya biya kuɗin magungunan da aka mata ,     Daga nan ya sake ganin likitan da ya bata taimako , ya sake yi masa bayani tare da sake jaddada masa a kula da lafiyar ta,  nan ya rubuta musu sallama zasu iya tafiya daga zarar an sake duba yanayin numfashin ta , A bakin ƙofa ɗakin ya tarar da rahima tana zaune ,    Da sauri ya tura ƙofar ya shiga idanun sa suka sauƙa akan ta , har yanzu tana zaune rungume da jaririyar da take ta bacci abin ta , waye anan ?  Tace tana sake rungume ƴar ,    Fatima , ya ƙira sunan ta muryar sa babu amo ,    Ƙwalla ce ta sake kawo mata a ido , ita dai wannan mutumin ya fi ƙarfin ta ,   Dan Allah , Dan Allah ka bar min ita , kar ka raba ni da ita ,   Shiru yayi yana kallon ta , idan har yace zuciyar sa bata yi laushi ba akan tausayin yarinyar ya faɗi ƙarya , Fatima za ki bi ni mu tafi ??  Za ki bi ni na tafi tare da ku ke da ɗiyar ki  ?? ? Inda take jin sautin muryar sa ta saita idanun ta tamkar tana ganin sa , Muryar ta ƙasa-ƙasa , ta juya tambayar kan sa , Za ka yadda na bi ka , ? Idan na bi ka za ka bar min baby a tare da ni ?? Idan za ki bi ni zan bar ki miki ita har abada a hannoun ki , babu mai raba ku ,! NA YARDA ZAN BI KA ,! **** ƙarfe huɗu suka dawo gida , numfashin falmata ya samu daidaito , tana maƙale da ƴar ta tsam , lokaci zuwa lokaci tana ɗan jijjiga ta saboda kukan yunwa da ta fara , Suna shigowa prof wanda tunda suka tafi yake ƙiran rahima ya ji halin da suke ciki , ya ji hankalin sa ya kwanta da ya ga falmata ta warware , kai tsaye falmata da rahima suka wuce cikin gida domin su haɗawa baby madarar ta , Shi kuma Biyamuradi ya shiga wajen prof ,    Cikin nutsuwa youssouf ya yiwa prof bayanin yadda suka yi da falmata akan amincewa da tayi zata bi shi , ya ɗora da cewa     Na ɗauki Alƙawarin zan kula da ita tamkar yadda zan kula da ɗiya ta , da yardar Allah ,    Gyaran murya prof yayi bayan ya gama jin sa ,     Ɗana ka so kan ka dayawa , kuma a wannan gaɓar inada ikon yin hani , saboda yarinya amanar Allah ce a hannu na , shi ɗa na kowa ne , abunda baza ka so ya samu ɗan ka ba idan kana da ikon hanawa kar ka bari ya samu ɗan wani , ni a matsayina na wanda wannan yarinya take a ƙarƙashin iko na a yanzu , bazan amince maka ka ɗauke ta ka tafi da ita ko ina ba , tana matsayin ƴa mace , kai ko namiji ce bazan yadda ba bare ƴa mace , to a wanne dalili ? Ka tafi da ƴar ka wannan ƴar ka ce ,kana da iko da ita  amma fatima kam baza ta bi ka ko'ina ba ! Shiru youssouf yayi kan sa a ƙasa , shi tausayin falmata yake ji matuƙa , sannan yana da kyakkyawar niyyar sauke ƙudirin sa na tun farko da ya so cikawa akan yakaka , a yanzu da bata nan zai so ya tallafi falmata , ko da babu baby mama zata samu taimakon sa sanadin yakaka ,! Baba ayi haƙuri a duba da kyau dai ita ɗiyar nan idan an raba su da jaririyar nan matsala ce babba zata auku , lafiyar ta abun dubawa ce ,   Babu alamun sassauci a muryar prof ya ce idan ka ga na bar ka ,  ka tafi da fatima , to ka ɗauke ta ne ƙarƙashin amincewar shara'a   amincewar shara'a ? Youssouf ya maimaita Ƙwarai ina nufin igiyar AURE ta ƙullu a tsakanim ƙu , ta zama halalin ka , ta maye gurbin ƴar uwar ta a gurin ka , to a lokacin kana da ikon da zaka tafi da ita tare da ƴar ka duk inda kake so cikin duniya ,bazan hana ba,  idan kuwa ba haka ba ka janye batun zuwa da ita ko'ina idan Allah ya kai mu gobe ka zo ka ɗau ƴar ka kamar yadda ka ce , na gama magana ! Ɗago kan sa yayi yana kallon prof tamkar  sassaƙen mutum mutumi , AURE ?     AURE TSAKANIN sa da wa ? Wannan ƴar ficiciyar yarinyar ? Ƙanwar yarinyar da yayiwa ciki ?  Makauniya ƴar gudun hijira ? Marar gata marar galihu marar dangi ??   Wani irin yanayi yake ciki akan tunowa da yayi da wacece ita , ? Bugu ƙirjin sa ya shiga yi gumi yana tsattsafo masa har yana ɗiga daga goshin sa duk kuwa da sanyin ac da ya wadaci falon , "   Youssouf mutum ne da yake jajirtatce mai kafiya akan cikar burin sa bai cika duban yadda gaba zata kasance ba idan yaso aiwatar da wani ƙudiri nasa , a yanzu tafiya da ƴar sa shine a gaban sa , so yake ya tsira da ƴar sa ba tare da ya bar baya da ƙura ba , ba tare da ya ci karo da wani abu da zai iya yi masa shamaƙi ba , raba fatima da baby mama wani abu ne da idan yayi , har abada baya jin zai iya mantawa kamar yadda ya riga ya san cewa tabbas idan ya tafi ƙasar su dawowar sa nigeria wani abu ne da yake gani da wuya ya kasance to ya dawo yayi me ?? Waye nasa a nigeria ?  Ba shi da kome a nan , bai taɓa zuwa ba sai ta dalilin aikin sa , Kalmomin da zuciyar sa ta riga ta amince masa da hukuncin da ya yanke sune suka jero kan su suka fito ta tsakanin laɓɓan sa , NA AMINCE DA AUREN TA ! a take fuskar prof ta yalwatu da haske da fara'a    Masha Allah Masha Allah haƙar sa ta cimma ruwa , Ka amince zaka auri fatima ƙanwar matar ka ??    NA AMINCE ZAN AURE TA ! Assalamu Alaikum ! Masu karatu , Da fatan duk kuna lafiya cikin aminci ? Ina sake miƙa godiya ta bisa ga tarin saƙonnin ta'aziyar ku da suka iso min kan rasuwar ƙani na , nagode ƙwarai Yaa Allah ya amsa addu'o'in da ku ka yi masa , ya kuma baku lada Ameen thumma Ameen    Nagode !      [9/3, 10:13 PM] +234 806 122 1116: Fikra writers association MAFARI ( Hargitsin Rayuwa ) umm'muaz 30 Babu kowa a harabar barikin sai masu gadi da suke daga kowacce kusurwa  , sakamakon dare da ya raba tsaka 2am , sai Biyamuradi youssouf da ke kai kawo a cikin hunturun sanyin da yake ratsa har ɓargon mutum gami da iska mai ƙura da take toshe ƙofofin hancin ɗan adam , a tsaye yake tsakiyar filin ya sunkui da kan sa jikin sa sanye da ƴar baƙar riga mai gajeren hannu da dogon wondon uniform ɗin su na soji , Ya zurfafa a tunanin makomar Auren da yake shirin karɓarwa kan sa nan da wasu ƴan awanni zuwa wayewar gari ,     Ina zai dosa da auren yarinyar ?? Yarinya ce ƙanƙanuwa , sannan kuma miskiniya , ta wacce hanya zai fara tallafar ta , domin ƙwarai take buƙatar matallafi cikin rayuwar ta da bata da kowa sai ƴar jaririyar sa ,     Me zai cewa iyayen sa su fahimce sa da dalilin sa na auren ta? Wanne irin hukunci maimartaba da hajiya umma zasu yanke masa idan suka ji ainahin abunda ya aikata da har ya kai shi ga auren yarinyar ?? Zasu su yi fushi mai tsanani da shi irin fushin da baya fatan ya gitta tsakanin sa da iyayen sa duk tsawon rayuwar sa ,     Me zai wakana tsakanin sa da gimbiya maimunatu lokacin da ta san ya auri wata mace kafin ita , Yana riƙe da auren wata bayan ita ? Zata iya yi masa kallon mayaudari kuma munafuki , a ƙarshe soyayyar su zata gurgunce da zai iya datse alaƙar su shi da ita , bai fatan haka saboda ya shaida irin tarin ƙaunar da zuciyar sa ke yiwa gimbiya maimounatu, Kalaman prof ya tuno inda yake ce da shi ,     Madallah tunda ka amince da auren Fatima , ka zo da wakilan/waliyan ka, a gobe zan baka auren ta , daga nan idan kana buƙata a goben zaka iya tafiya da ita tare da ƴar ka ,    A lokacin ya amsa masa da     Toh na Amince Har ya tashi zai tafi prof ya tsaida shi , To amma akwai wani lamari guda ɗaya , lamarin kuwa shine bazan iya ɗaukar yarinyar nan na baka ita , ka tafi da ita, ita kaɗai ba dole zan haɗa ka da mutum ɗaya wanda za ku tafi tare chan ƙasar ta ku domin a gano inda zaku zauna saboda sha'anin duniya , ta ka zo ta kan zo ko watarana wasu daga cikin dangin su zasu ɓullo su zo neman sanin inda ƴar su take , da fatan ka fahimceni da kyau kuma ka amince ?    Jim yayi a ƙarshe ya sake amsawa da    NA AMINCE Waje ya samu ya zauna akan ɗaya daga cikin dakalin da aka yi su domin zama dake a watse cikin barikin , Da farko yayi niyyar idan ya ɗauke ta ya kai su Niamey gidan ubbo a matsayin ƴar gudun hijirar da ya taimaka ita da baby mama idan ya so su kasance ƙarƙashin kulawar ubbo tare da shi har zuwa lokacin da zai samawa kan sa hanyar da zai bi ya bayyana su ga dangin sa ba tare da abubuwa sun rinchaɓe masa ba , Sai dai batun haɗa su tafiya da wani ya rusa wannan nufin nasa domin ko kusa ba zai so a san wasu dangi nasa ba , ba zai so asan ko shi wanene ba saboda kar watarana kome ya bayyana , a biyo sawu ba tare da sanin sa ba , kome ya lalace masa a lokacin , Idan kuwa har ya nuna ƙin amincewar sa , hakan zai sa a dasa ayar tambaya akan sa , ayi masa zaton marar gaskiya , wanda zai iya sa pro ya tsananta bincike akan sa wataƙila a ƙarshe kome ya isa ga masarautar su , bai fatan haka , Idan kuwa haka ne dolen sa ya yarda ya tafi da su da me rakiyar su , Ƙaunar ƴar sa da Allah ya jarrabe shi da shi ya sa duk yana ƙoƙarin fuskantar duk wani ƙalubale , burin sa ya tsira da ita , dan haka a ƙarshen tunanin sa ya ture duk wani ƙalubale gefe ya amince da mallakar baby mama tare da uwar goyon ta a lokaci guda da me rakiyar su , Yana tsaye a wajen aka yi ƙiran sallan farƙo na karfe 3:30am , kai tsaye ya nufi babban masallacin cikin barikin ya ɗaura alwala da sassanyan ruwan da iskar hunturu ta gama hura sa ya shiga masallaci ya fara jero nafilfili , yana roƙon Allah ya bashi nasara akan manufar sa ya kuma rufa masa asiri ya kawo masa warwaruwar al'amuran sa a sauƙaƙe , "toh ameen," ALƘAWARIN UBANGIJI ( MATAR MUTUM DAGA GARE SHI TAKE ) Da misalin ƙarfe goma na safiyar ranar Alhamis ɗin karshen sati ,  ƴan tsirarun mutanen da prof ya ƙira na cikin unguwa da basu wuce goma ba tare da wasu ƙarin mutane biyar da youssouf ya kawo a matsayin wakilan sa wanɗanda a zahiri abokan aikin sa ne daga ƙasar su , suka haɗu suka shaida ɗaurin auren FATIMA DILMARI , tare da YOUSSOUF ABDUL-AZIZOU BASKORE , wanda ya sauya suna zuwa youssouf Garba Malbaza Uzine, Bayan ɗaurin auren babu ɓata lokaci su abokan aikin youssouf suka yi komawar su domin ɗaura shirin tashin su zuwa Abuja inda zasu wuce ƙasar su ta jirgin sama a yau ɗin ,,  da shi kuma youssouf ya shigar da neman iznin a bada mota guda cikin motocin su na soji tare da direba da zai tuƙa su zuwa Niamey ta hanya , ba'a tsananta bincike ba aka bashi izni tare da shaida masa ya tabbatar ya samu isa niamey kafin ranar litinin inda za'a yi bikin dawowar su tare da yi musu ƙarin girma , Hajja me wurya," ita ce dattijuwar da prof ya zaɓa a matsayin wacce zata raka fatima ɗakin mijin ta daganan ta gano garin da zasu zauna a niger , kasancewar ita hajja mai wurya dattijuwa ce da a ƙalla ta tasamma shekaru hamsin , sannan kuma a halin yanzu bata da wani jigo cikin rayuwar ta iyaye duk sun mutu dangin kuwa kowa ta kai ta kai yake sannan tun asali bata da haula ɗan ta ɗaya ne tal da ta haife shi a shekarun girma bayan aure auren da tayi ta yi domin neman haihuwa , tana tsakiyar fara cin moriyar ɗan nata da ya ɗan fara tasawa shekarun sa ishirin da huɗu , ƴan tawayen boko haram suka shigo har gida suka yanka mata shi , a cewar su yana zagin su tare da sukar akidar su , dan haka suka kawar da shi, Tun daga nan rayuwa ta fara yi mata wahala , ƙunci da talauci suka dirar mata , zamani ne da kowa yake gudun wahala ba'a duban zuminci , tunda ta fahimci haka ta daina yin raragefe gidan ƴan uwa ta bazama neman na kan ta sanin da tayi da ɗan sauran karfin ta bata zama ƙarƙashin dangina ana zuba mata sharar walakancin , aikatau ta fara a gidajen saida abincin ,kasancewar ta gwanar girki iri iri ,musamman ma na ƙasar camaru da tayi farkon zaman auren ta a chan ,  amma sakamakon tsaurin ta da kuma tsayuwar ta kan gaskiya ya sa ba ta cika daɗewa a wajen aikin  ake sallamar ta , saboda bata zuru duk ta ga zalau sai ta tsinka ,"  daga baya ta koma aiki a gidajen masu hali nan ma gida biyu tana barin aiki saboda yadda take gwadawa uwargida iyakar ta a cikin gidan ta idan har ta ga abunda bai dace ba,  sai fa wannan karon da tayi dace ta samu aiki gidan Professor Mustspha dilmari  Allah ya tsawaita zaman ta a gidan da taimakon tarbiyyar yaran gidan da basu cika raini da walakanci irin na sauran ƴaƴan masu hali takwarorin su ba , babu kuma matar gidan shekaru biyu take nema da fara aiki a gidan a matsayin mai yin girki , musamman ma na shi prof . A jiya da prof ya ƙira su ita da falmata ya faɗa musu hukuncin da yake ƙoƙarin yankewa har ma ya tuntunɓi ita falmata akan jin ra'ayin ta , ta amince zata auri baban ƴar da take riƙo su tafi ita da shi da ƴar chan ƙasar sa ko kuwa ?? Ga mamakin sa ba tare da shayin kome ba Falmata ta amsa da ta amince zata auri baban baby ya tafi da ita tare da baby ,    Ƙwarai prof ya ji daɗin amsar Falmata domin da farko har yana fargabar ko yarinyar zata ƙi gatan da yake son yi mata na aurar da ita tunda ƙuruciyar ta , ga mutumin da yake iya hango nagartar sa a cikin yanayin sa da mu'amalar sa , yana hasashen mutum ne na ƙwarai ! A sarari ya nuna jin daɗin sa tare da yi mata addu'o'in samun nasara a rayuwa , sannan ya juya ga hajja mai wurya wacce ita ma take durƙushe daga gefen falmata , Hajja Alfarma zan nema a gurin ki akan ki raka fatima ɗakin mijin ta ki gano min wajen da zasu zauna ita da mijin ta a chan niger ɗin daga baya sai ki dawo. Da fatan zaki min alfarma ? Dariya hajja me wurya ta sa ! Babu kome Alhaji zamu tafi tare , me zaman aure ma ta amince bare ni ƴar rakiya ?? Ai ko gaba da binnin sin ne Alhaji ba na ƙi raka ƴar marainiyar Allahn nan ba , kai shima dai wannan dogon balaraben nijar ɗin Allah yayi masa Albarka da duk da kyan nan nasa da cikar zati irin ta ɗa namiji amma haka ya runtse ido ya ce ya amince zai auri wannan murɗaɗɗiyar bahaguwar yarinyar , ai dole ayi masa godiya bawan Allah . Nan dai Alhaji ya sallame su yana sake musu godiya akan biyayyar da suka ma sa , Kan hanyar su ta komawa hajja mai wurya tana riƙe da hannun falmata tace    Ke ƴar nan Allah ya dube ki ya tarfawa garin ki nono , irin wannan zankaɗeɗen miji da Allah ya wanke ya ba ki ?? Ai ko ɗiyar masu mulki ba ta ƙi shi ba , to zan fara faɗa miki tun wuri tun yanzu , ki zubar da waɗannan hargitsatsun halayen naki tun a nan nigeria kar ki ce zaki tafi gidan auren ki da su , saboda wannan dai miji naki wallahi kin yi sa'a wanke hannun ka taɓa Allah dai shi sa yadda surar nan tasa take halin sa yafi haka kyau , Ai bazan bar gidan nan naki ba sai na ga kamun ludayin zaman naki da shi , ato sai ki shirya ni ɗin dai da kika tsana kike ƙin bani riƙon jaririya , nice dai me miki zaman ɗaki sai dai muyi wacce za mu yi mahaukaci ya ɗau rigar kurma ... Zame hannun ta tayi daga cikin na hajja tayi gaba ta miƙa hanya , ƙalau tamkar me gani saboda yau da gobe ta fara haddace hanyar a ƙwaƙwalwar ta,    Sasakai hajja me wurya tayi    Au aikin banza kenan hanci ba ƙafa , to ki fi ruwa tafiya , nace ki fi ruwa tafiya , wannan yarinyar sai na dage kafin ta shiga hanya ta ɗau haske ta san me duniya take ciki kan ta hayaƙi yake ,! Falmata ko sauraron ta bata yi ba hasalima ji tayi hayaniyar hajja me wurya ta hana kwakwalwar ta sakewa tayi tunanin da ya kamata shi yasa ta zame hannun ta ta rabu da ita ,    Aure da ita da shi ?? Wanene shi da yace baban baby ne ? Da gaske shine baban baby ? Wanne irin aure zasu yi ? Ina ne ƙasar ta su ? Idan suka tafi zasu dawo ? Bata son barin nan inda take , burin ta watarana dr hamza ya nemo mata maman su , to amma yanzu kuma ga shi zata tafi ta bar nan ɗin ,     Abun da ta sani zata yi kome , zata tafi ko ina zata kuma ta shiga kowannen wahala domin ta tsira da baby mama , domin ta tsaya tare da baby mama , domin baby mama kar ta sha wuya , naƙasun ta miskinancin ta , rashin idanu , da ace ita lafiyar ta ƙalau , bata buƙatar abokin tayi wajen gina rayuwar ƴar ta , da zata gudu da baby mama ta ɓuya wani waje tana kula da ita , to amma ita ɗin ma miskiniya ce dole ne ta bi baban baby da yace zai kula da mama ƴar sa ce ! Ƙarfe biyu cif aka fara fito da jakar bocco ɗin falmata wacce ta haɗe kayan ta da na yakaka kakaf a cikin babbar baccon yakakar , sai kuma kayan baby mama shima a cikin babbar jaka , duk aka zuba su a bayan dunƙulalliyar motar soji me ƙirar golf kofa biyu , Biyamuradi youssouf ya taka zuwa cikin gidan falon prof , suka yi sallama inda prof ɗin ya bi shi da kalaman godiya ya kuma ɗora da damƙa masa amanar fatima tare da roƙon sa akan ya kula da ita , ita ɗin abar a tausayawa ce , Nan youssouf ɗin ya amsa tare da ɗaukar Alƙawarin zai kula da ita , Yana zaune hajja me wurya da falmata rike da mama haɗi da rahima suka shigo , falmata tana shirye tsaf cikin sabuwar atamfar ta ruwan ganye da adon furanni farare,  ta saka farin hijabi har guiwar ta , Daga gefe suka tsugunna , nan prof yayi musu addu'o'i tare da ƴan nasihu ya sake ɗanƙa amanar falmata a hannun hajja me wurya har lau , Daga ƙarshe ya zaro kuɗin sadakin falmata naira dubu ishirin sabbin bandir ɗin ƴan ɗari biyu ,    Ungo Rahima , miƙawa fatima kuɗin sadakin ta hakkin ta , fatima ina me baki haƙuri akan yadda auren ya zo a ƙurarren lokaci ban miki kome ba da iyaye ke yiwa ƴaƴan su idan zasu kai su gidan miji , amma na miki alƙawari na kuma yi magana da shi mijin naki akan idan kun isa ya tura min account number zan tura da kuɗin da za'a saya miki kayan ɗaki da na amfanin gida a chan kin ji ko ? Ki riƙe wannan sadakin auren ki ne , Da sauri falmata wacce idanun ta suka kawo ruwan hawaye akan irin ƙaunar da prof ke musu tare da sanin cewa yau zata bar gidan shi zuwa wani waje da bata da sani akan me zata je ta tarar , tace   Baba na bar maka kuɗin ni babu abunda zan yi da su ,   A ah fatima ki karɓa nace hakkin ki ne , watarana zaki samu abun saya da su ,   Muryar ta na karkarwar kukan da ta soma tace   Baba to ka riƙe min idan na dawo zan karɓa , Ba shiri hajja me wurya ta zungure ta , tana satar kallon youssouf da yayi shiru yana sauraran ta ,    Ƙasa-ƙasa tace   Ka ji min sakarya auren da tun baki kai gidan ba kike fatan ki dawo , ?? Kawo ƙuɗin na riƙe mata Rahima, irin kunyar nan ce ta amare take gwada mana ,    Rahima da take murmushi a hankali ta miƙawa hajja me wurya kuɗin , Madallah Allah ya sanyawa auren ku Albarka Allah ya sa abokiyar arziki ce , Allah ya kauda shaiɗanun aljanu da na mutane a tsakanin ku , Allah ya sa mutuwa ɗai ita zata raba ku, Allah kuma ya baku zuri'a masu albarka irin wacce manzo Allah zai yi alfahari da ita !     Laɓɓan Youssouf ne suka motsa a hankali da ,"Ameen .     Rahima ita ta raka su har bakin mota tana jin yadda kewar su take taso mata , ai anyi sabo zaman watanni tare , duk da cewa ta so tafiyar su tafi haka tsawo sai dai damar bata samu ba , amma ko babu kome tayiwa fatima murnar samun ɗanɗasheshen mijin da ya ƙere sa'an auren ta ta ko'ina hakkun fatima me sa'a ce .     Da wannan tunanin ta rufe musu ƙofar motar bangaren da falmata ta shiga inda suke zaune tare ita da hajja me wurya a bayan motar , Biyamuradi da direban sa suna gaba ," . ***** Tafiya ce suka ɗora ta miƙaƙƙiya tun daga maiduguri zuwa sokoto , inda basu samu isa sokoto ba sai cikin dare misalin sha biyu da rabi , alamun gajiya da suka bayyana baro-baro ga falmata tare da baby mama wacce ta ke yin ƙananun rikici na gajiya da rikon hannun ya sa youssouf ya kama musu ƴan ɗakuna a wani ƙaramin guess inn da yake cikin garin na sokoto zuwa wayewar gari sun huta sun kuma sake shiri sai kuma su faɗa yankin niger ta," ilela ," su ɗau hanya ta birnin N'konni da zai ɗaura su kan kodoben da za su sadu da birnin Niamey ɗin niger ....! Ba su suka samu isa Niamey ba sai ranar Asabat da misalin ƙarfe bakwai na dare duk kuwa da gudun da direban ya dunga shararawa tun da suka faɗa yankin niger kasancewar sun shigo ƙasar su , kowa yaga gilmawar motar su basu hanya ake , Kai tsaye direban ya wuce da su ( Radisson Blue hotel,) ƙarƙashin umarnin youssof , kasancewar shahararren hotel ɗin mafi yawan lokuta nan ne wajen sauƙar sa idan wani aiki ya kawo shi Niamey ɗin kasantuwar hotel ɗin kusa yake da manyan ma'aikatu masu muhimmanci na ƙasar da ke babban birnin Niamey , Babu ɓata lokaci ya kama musu ɗakuna inda hajja me wurya da falmata zasu zauna a ɗaki guda , (one bedroom Residence ) dake ƙasa shi kuma ya Kama nasa ɗakin a sama ( royal suite ) inda ya saba zama idan ya zo otel ɗin yayin da direba yayi tafiyar sa inda sauran abokanan aikin su suke ,  ya bar masa mukullin tare da motar , ' Bayan yayi wanka ya sallaci isha'i , misalin ƙarfe takwas da rabi ya sauko ƙasa , ɗakin da suke ya tasamma , ƙwanƙwas musu ƙofa yayi , Hajja me wurya tana sallar isha'i lokacin , falmata kuwa ta idar tana kwance bisa faffaɗan gadon ta sanya baby mama a gaba wacce take ta baccin gajiya bayan an cika mata ciki da madarar ta me ɗumi , Sake ƙwanƙwasa ƙofar yayi a karo na biyu yana sake kallon number ɗakin da take rubuce a jikin wani ɗan katako dake sakale a jikin ƙofar  ,"nan ne dai ɗakin nasu ," Miƙewa zaune tayi     Hajja kamar ana buga ƙofa ko ? Ƙyat ! Ƙyat    Hajja ta mata alama da hannu Oho sallah kike ? Sake bugun ƙofar aka yi da ɗan ƙarfi da ya sanyata miƙewa a hankali bayan ta zura hijabin ta , Ƙasantuwar ɗakin ba wani babba sosai bane taku kaɗan tayi ta isa jikin bango , dan haka ta fara shafawa bata sha wahala ba hannun ta ya sauka jikin ƙofar,     Waye ne ?    Ni ne buɗe min ƙofa     Ta shaida muryar sa   kama mariƙar ƙofar tayi ta murɗa sai dai bata ji alamun ƙofar ta buɗu ba , Ban iya ba   tace da shi cikin ƴar ƙaramar muryar ta ,    ,'Bata iya buɗe ƙofa ba ? Ya tambayi kan sa ,"   Hajiya batta cikin ɗakin ??   Tana sallah ,      ta ce masa   Bai ce kome ba ya gyara tsayuwa gami da jingina da jikin bangon ɗakin ,    Cigaba tayi da tsayuwa tana ɗan laluba jikin ƙofar ko zata ji wajen buɗewa ,    Ba'a ɗauki lokaci ba hajja ta idar da sallah ,     Ke kam wannan yarinya anyi bagidajiya , yanzu ace buɗe ƙofa ma kin kasa ? Ni gusa ki ban guri ,   buɗe masa ƙofar tayi ya shigo suka gaisa ,     Hajja akwai abunda kuke buƙata ne ?     Babu abunda muke buƙata ɗan nan , mun gode ƙwarai da hidima ,    Idon sa ya ɗora kan baby mama ,     Ta daina rigimou kou ? Ba ku buƙatar kome kou ? Shiru falmata tayi domin bata ma san da ita yake ba , Hajja ta ce fatima maigidan na magana       Wanne maigida hajja ?? Wata ƙatuwar harara hajja ta wurga mata , tamkar falmatan tana ganin ta  a ƙufule tace     Baban jaririyar ta ki A sanyaye ta ce me yace ? Wai zai tafi da baby ?   Da sauri youssouf yace Ban faɗi hakka ba fatima cewa nayi ba ku buƙatar kome ? Eh !    Ta bashi amsa tana zama bakin gado ta shiga laluben baby mama, hannun ta ya sauka bisa kan ta ta shiga shafawa a hankali , Ya juya ga hajja , ni zan shiga gari wajen aiki na , akwai yiwuwar gobe sai yammaci zan shigo , duk idan kun buƙaci wanni abu ku ƙira ma'aikatan otel ɗin ta kan wayar tarho ,   Ga ta nan ," ya nuna mata telphone ɗin dake ajiye daga saman ƴar durowar gefen gado  " madallah hajiya ina sake godiya Mune da godiya ai ɗan nan mune da godiya , to to babu kome Allah shi taimaka muna nan muna addu'a Ameen hajja sai gobe    Ya juya yana barin ɗakin Da sauri hajja ta zunguri falmata ,     Ke baki san ki gaishe da miji ko kiyiwa miji addu'a bane ? yau ni hauwa'u na ga abunda ya fi ƙarfi na me zan gani haka ? Yanzu ashe haka za ki dunga gwada rashin hankali a gidan auren na ki ? Ko kuwa taƙamar yarinta kike ? To bari ki ji na faɗa miki ni lokacin da aka min auren fari ma ban kai ki cika ba , kin fini ƙugu da ƙirji da sharaɓa da kome ke har shekaru ma domin ni lokacin da aka min aure ma sha huɗu nake ko nonon arziƙi bani da su , amma billahil azeem ban yi irin wannan haukar da na hango somi-somin ta a tare da ke ba ,     Ke kenan sai ƙwalafacin ƴa , alhalin kina gwadawa uban ta halin ko in kula , idan taƙamar ki son ƴaƴa ai sai ki kwantar da kai kema ki samu ki tara naki ba ki dunga gwada naci akan ƴar wasu ba ,    Falmata wacce ta fara jin haushin hajja akan takurar da ta ke mata,  muryar ta a cunkushe tace ,   To a ta ya zan tara nawa ƴaƴan ??     Sororo hajja tayi ,   Ah lalle abun naki na yi ne,  'an biyawa bazaura hajji , to sai ki cigaba da tambaya ta , ranar bada amsa tana zuwa , aikin banza yarinya sai sokonci kika iya ,.    Washegari biyamuradi youssouf bashi zaune bashh& har sai da ya samu wani ɗan madai-daicin gida irin wanda yake so a unguwar ,(Banifandou 2) ya kamawa su falmata hayar sa ya biya kuɗin shekara guda cif , Ƙarfe hudu tayi masa a shahararren company ƙera kayan katako da shirya gida ,(sunwe) inda ya faɗa musu buƙatar sa na son a kai masa kaya dai-dai da tsari da fasalin gidan sa , Basu yi ƙasa a guiwa ba suka tashi ma'aikatan su har su huɗu suka je ganin gidan , Hotunan gadaje , kujeru da sauran kayan adon gida aka dunga nuna masa tare da kuɗaɗen su , Bai yi zari ba ya zabi dai-dai kudin sa , tare da matsayin Falmata a wajen sa , Ma'aikatan da kan su suka kwashi kayan a motar su zuwa gidan inda gobe zasu je su shirya kayan da safe , Sai sha biyun dare Youssouf ya koma hotel ɗin saboda tun ƙarfe takwas na dare yana tare da manyan su suna wata ganawa ta musamman da lieutenant-Gènèral da Major Général , waɗanda sune ƙashin bayan samun ɗaukakar sa a fannin aiki , Ya so ya je ya ga ɗiyar sa da yadda suka wuni amma ganin yadda dare ya riga yayi  sai ya yi wucewar ɗakin sa kai tsaye , da zummar gobe zai gana da su cikin rashin sanin sa yini baby mama tayi da matsanancin zazzabi tare da mura , banda kuka babu abunda take , tun falmata na rarrashi ita kaɗai har hajja ma ta karɓa , duk da haka ta ƙi shiru , zuwa dare har shiɗewa take gaba ɗaya hankalin su ya gama tashi banda kuka babu abunda falmata take ko abinci sun gagara ci , Ganin duhu ya sawo kai ga youssouf bai zo ba ya sa hajja me wurya fitowa daga ɗakin ba tare da ta san takamaimai ina zata nufa ba , Allah ya taikaita mata wahala ya gama ta da ɗaya daga cikin ma'aikatan otel ɗin da ya kawo musu abincin rana , Nan ta tsaida shi ta tambaye shi ina ne ɗakin wanda ya kawo su ? Suna buƙatar taimakon sa , bai gane inda ta dosa a maganar ta ba saboda haka ya yi mata jagora zuwa gun manyan su , inda cikin kwatancen hajja me wurya tare da duba sunan ainahin wanda ya kama musu ɗakin da suke suka fahimci colonel youssouf take nema , basu da number wayar sa dan haka suka shiga ƙiran layin telfo na ɗakin sa nan ma basu ci nasara ba domin wayar tana ta ƙara ba'a ɗauka alamun da ke bayyana babu mutum a ɗakin . Ganin yadda hajja ta damu tare da sanin matsayin wanda ya kawo su ya sa suka tambaye ta matsalar su ? Nan ta shaida musu ƴar shi wanda ya kawo sun ne jaririya bata da lafiya suna neman a kai ta asibiti , Nan take ma'aikatan hotel ɗin suka jagorance su zuwa wani asibiti me zaman kan sa mafi kusa duba da halin da ƴar jaririyar take ciki na wahalar numfashi, bayan sun haɗa su da likitoci da nan take suka karɓi baby mama suka fara bata taimakon da ya dace , Sai suka dawo suka cigaba da ƙiran layin ɗakin youssouf lokaci-lokaci ko ya dawo ? Dan haka da shigar sa ɗakin bai rufa mintoci goma ba fitowar sa daga wanka kenan , kan wayar ɗakin ta fara ƙara , Nan ya ɗauka bayan sun gaisa suka sanar da shi halin da ƴar sa ke ciki tare da asibitin da suka kai ta , A gigice youssouf ya sanya kayan sa gami da ɗaukar ɗan mukullin motar sa , kai tsaye ya tasamma asibitin da ba baƙon sa bane domin fitatcen asibiti ne da duk ƙasar aka san sunan sa ,! Bai wani sha wahala ba illa tashin hankalin da yake ciki lokacin da ya samu ganin babban likitan da aka tabbatar masa shi ya kula da jaririyar a daren , A kiɗime youssouf ke tambayar sa ina ƴar ta sa take ? Kuma a wanne hali take ciki ? Nan likitan ya kwantar masa da hankali inda ya shiga yi masa bayanin abunda ke damun ƴar sa  tana da ,( single pneumonia )  wanda kuma shi ya kawo mata wannan wahalar numfashin tare da zazzaɓi me tsanani , sanadin shaƙar ƙura me ɗauke da ƙwayoyin cuta da tayi, Dan haka likitan yayi ƙira da a kiyaye sosai a kula da ita , a ƙarshe ya sanar da shi an shawo kan matsalar ta a halin yanzu har ma ta samu bacci zuwa gobe idan aka ga yanayin jikin ta ana iya sallamar ta , Tare da likitan suka nufi ɗakin da aka kwantar da baby mama ɗaki ne na musamman ( side room ) inda falmata da hajja suke tare da ita , Lokacin ƙarfe ɗaya saura na dare dan haka nuna masa ɗakin ya yi , ya juya , A hankali ya murɗa kofar ɗakin ya shiga , da haske wal a ɗakin dan haka ya hango falmata daga kan gadon tana zaune ta jingina bayan ta da jikin ƙarfen gadon tana riƙe da baby mama a hannun ta , ga alama bacci take , Hajja kuwa tana kwance akan ƴar shimfiɗar da ma'aikatan asibitin suka bata sai sharar bacci take saboda gajiya da tayi da kuma jikin girma ! A hankali ya tako cikin ɗakin ya ƙarasa bakin gaɗon gami da rage tsawo ya leƙa fuskar baby mama , ya yi haka ne saboda baya son tashin su a bacci, Falmata kuwa tun taɓa ƙofar da yayi ta ji sa , hasalima ba nisa baccin na ta yayi ba saboda sam yanayin wajen da yayi shiru sosai yana bata tsoro , tun tana ƙiran sunan hajja lokaci zuwa lokaci tana amsa mata har dai ta ji hajjan tana mitar ta dame ta da ƙira cikin magagin bacci dan haka ta haƙura ta ƙyale ta , Tayi shiru tana sauraran sauƙar numfashin baby mama da take yin sa cikin nutsuwa alamun sauƙi ya samu gare ta , Hannun sa ya kai a hankali da nufin ƙara rufe jikin baby mama da ya ɗan buɗu kaɗan ba tare da sanin falmata ba , Yana ajiye hannun sa ta maida nata akan nasa ,    Ɗago kan sa yayi ya dubi fuskar ta , manyan idanun ta da suka ɗan yi jaa kaɗan sun kafe fuskar sa da kallo tamkar tana ganin sa ,    Haɗa baki suka yi wajen yin magana ƙasa-ƙasa    Ita tana tambayar wanene ?   Shi kuma yana cewa ni ne fatima ! A hankali ta ɗauke hannun ta daga kan nasa ,   Shi kuma ya gyarawa baby rufuwa tamkar yadda yayi niya cikin ran sa yana mamaki tare da girmama nisan kunnen ta tare da yadda take kaffa-kaffa da ƴar baby , da ɗai bai taɓa cin karo da uwa irin ta ba , duk da ƙarancin shekarun ta Komawa yayi ya zauna akan ɗaya daga cikin kujerun wajen yana duban fuskar ta cikin nazari , kallon ƙurr yake mata tsaf yana wasu tunaninnika masu nissa , A jikin ta take jin idanun sa suna yawo saboda tsikar jikin ta da ta ji tana mimmiƙewa,! ya tsinkayi muryar ta da ɗan karfi tace .    Ka ɗaina kallo na haka bana so ! Ware idanu yayi da ɗan mamaki a fuskar sa ,"ya aka yi tasan ina kallon ta ,"? kafin yayi murmushi kaɗan ganin yadda ta turɓune fuska , ,'Ƴar baiwa ce," ya aiyana haka cikin ran  sa , a sarari kuwa cewa yayi     Ki kwantar da itta ke ma ki kwanta dare yayi ,!       Yayi baya da kan sa tare da miƙe dogayen kafafun sa ya ɗan zame kaɗan akan kujerar yana jin yadda tunanin lamura suke yi masa rubdugu tamkar yadda ya saba duk dare tunda abubuwa suka fara haɗe masa ! ***** Stade Général Seyni kountchê ( SGSK ) nan ne babban filin da gwamnati ta shirya gudanar da bikin karamma sojojin ta waɗanda ta tura nigeria tare da yi musu ƙarin girma , har ma da kyautuka ga waɗanda suka chanchanta , ! Mai martaba sarkin Maradi tare da Mommoudou , 'wanda hajiya mama ta tilasta masa zuwa taron ƙarin girman ," sai Tafeeda ƙarƙashin rakiyar tawagar maimartaba , suna cikin mutanen da suka halarci wannan taron da suka samu isowa a yau , sai kuma Ubbo tare da Siyama wacce ita ma ta iso Niamey tun ranar asabat tayi zango a gidan ubbo tare da cigaba da tsara yadda zata fara bin matakin farko na kusanta kan ta ga Biyamuradi muradin zuciyar ta ! Da wasanni irin na soji , kiɗe-kiɗen su zuwa faretin su , aka fara buɗe taron da kai tsaye ake watsa shi a gidajen tv dake baki ɗayan ƙasar Niger , Kafin a bada dama ga maigirma Shugaban ƙasa yayi jawabin yabo da jinjinawa ga sojojin ƙasar sa , sannan shugaban rundunar sojojin ƙasa na ƙasar ma yayi nasa bayanin , har zuwa kan wasu manyan kusoshin gwamnatin ƙasar da manyan soji da duk dai yabo ne suke yi ga sojojin su da suka dawo daga bakin daga , Youssof Abdul-azizou shine wanda aka fara ƙira domin martaba shi tare da yi masa ƙarin girma , Da faretin su na soji ya fito filin ya ƙarasa har zuwa gaban shugaban ƙasa ya sara masa ya juya gaban manya-manyan sojojin su na ƙasa nan ma ya sara musu kafin ya ƙarasa kan ɗan tudun da aka tanada domin tsayuwar sa inda shugaban sojin su na ƙasa yake tsaye , daga gefen sa wasu sojoji biyu ne a ƙame da ƙwali rike a hannuwan su  , Sara masa yayi ya ƙame , cikin takun sa na soja lieutenant General ya ƙaraso gaban youssouf tare da kai hannun sa ya warware ɗan yadin dake ɗauke da tambarin girman matsayin youssouf ɗin a soja , ya miƙa sa ga ɗayan sojan dake hannun sa na hagu ya sa a kwalin hannun sa , lokaci guda ya waiga ga ɗayan sojan ya ɗauki sabon rank ɗin da ke ɗauke da zanen yellow layi huɗu wanda yake ninke cikin kwalin hannun sojan ya maƙala a gefen kafaɗar youssouf ɗin dai-dai inda ya cire na farkon , Da hakan yake nuni da sabon matsayin Youssouf Abdul-azizou Baskore da ya tashi daga colonèl ya koma MAJÓR YOUSSOUF ABDUL-AZIZOU BASKORE , A take gurin ya ɗauki tafi tare da sarewa da gangunan su na soji , wani irin yanayi ne ya bayyana a fuskar mommodou da take kirtiɓ ya haɗe girar sama da ta ƙasa , idanun tafeeda da ya sauƙa cikin nasa shi ya sa shi gyara yanayin fuskar sa tare da haɗa hannunwan sa biyu cikin yanayi na dole ya ɗan tafa su ,! Da fareti major youssouf ya dunga bin su ɗaya bayan ɗaya tun daga kan shugaban ƙasa har zuwa shuwagabannin sa wajen aiki yana sake sara musu , masu camera na aikin haska shi da masu ɗaukar sa a  video ,  ƙarshe ya dire a gaban mahaifin sa da yake hakimce cikin shigar su ta sarakuna , idanun sa da suke sakaye cikin farin gilashin ƙarin ƙarfin ido suna bayyana tsantsar farin cikin da yake ciki , yayin da bakin sa da yake rufe ta cikin rawanin sa yaƙi daina murmushi , Ƙamewa yayi ya sarawa mahaifin sa , ga jin daɗin sa sai maimartaba ya miƙe gami da miƙa masa hannu suka yi musabaha idanun su na musayar zallar ƙauna , ya rungumo shi zuwa jikin sa ,    Bakin sa na furta kalmar   MADALLAH DA KAI MAJOR YOUSSOUF KAI KA KASANCE ABUN ALFAHARI NA ,    Kunnuwan youssouf kaɗai suka jiyo me mahaifin nasa ke cewa . Yayin da fuskar mommodou tayi jaa tana tsattsafo da gumi . Ware idanu sosai hajja me wurya take cikin son tabbatar da fuskar wanda take gani tarwai a fuskar ƴar tv da take kunne cikin ɗakin su na hotel da basu fi mintoci ishirin da dawowa cikin sa ba daga asibiti da aka sallamo baby mama wacce tayi sumul da ita tana ƴan wasanni ta tamkar ba ita ce jiya ta sha wahala ba ,    Ke fatima wannan ba mijin naki bane ake masa ƙarin girma a wajen aikin sa? Ga shi nan ana nuna sa a tv,?  ashe babban SOJA kike aure , ah ki ce shiyasa kike firirita , ashe matar soja ce ,    SOJA ? waye ne sojan ? Ita fa bata ƙaunar soja ko jin sunan su ta yi zuciyar ta tsinkewa take , mutanen da suke da bindigogi da jiragen yaƙi ita kuwa ai bata manta bama-baman da sojoji suka dunga sakar musu a daji ba, da har ya sa ta gurɗe ƙafar ta gurin gudun ceton rai ,   Saitin inda take jin tashin tv ta maida hankalin ta kafin ta ce    Hajja waye ne soja ? Shi baban jaririyar taki , Gwalalo idanu tayi   Soja ne daman ? Soja masu ƴaki da bindiga da jirgin ƴaki hajja ? Au daman baki ma san irin aikin mijin naki ba ? Hunm abun naki sai ido , bebiya ta auri makaɗi , Shiru falmata tayi tana jin wani tsoron sa sabo dal yana ɗarsuwa a ran ta , baban baby SOJA ne ?, " **** La'asar tayi musu a gidan da yake matsayin na biyamuradi youssouf da falmata , sojan da ya kawo su niamey shine ya je ya ɗauko su daga hotel ɗin ƙarƙashin umarnin youssouf da tun safe suke tare da maimartaba tare da wasu manyan ƙusoshin ƙasar a ainahin cikin gidan gwamnatin tarayya , Tunda suka shigo gidan da bayan sojan ya gama shigar musu da kayan ya danƙa ƴan mukullayen ga hajja me wurya ,   Santin gidan hajja take tana bin kowanne lungu da saƙo tana leƙawa tare da addu'o'i tana jere su iri iri , Gidan ba wani babba bane amma tsarin sa me kyau ne dai-dai da rayuwar mai rufin asiri kuma ƴan gayu , ɗakuna uku ne a cikin dan madaidaicin falon sai kuma kitchen da yake ta cikin falon sai keɓantatcen wajen cin abinci , ko'ina an sanya kayan da suka dace , cikin ɗakuna biyun gadaje ne iri ɗaya tare da wardrobe ɗin su,  sai dai ɗaya ɗakin akwai set ɗin gadon jarirai har da ƴar kwabet ɗin jera kayan jarirai da yake mallakin baby mama , gidan kam yayi kyau sai sa albarka hajja me wurya take , ita kaɗai ba tare da falmata ta kula ta tanka mata ba , yammaci lis biyamuradi Youssouf ya iso gidan tare da shi akwai sabon direban da gwamnati ta ba shi , bayan motar su cike taf da kayan abinci zuwa ƴan kananun kayan buƙatu na gida irin su , omo , sabulai , toothpaste d a sauran su,  Kai tsaye ya shiga gidan bayan ya ƙwanƙwasa ƙofa hajja ta buɗe masa , kan ɗaya daga cikin kujerun falon ya zauna bayan sun gaisa da hajja wacce take ta shi masa albarka har ma ta taya shi murnar ƙarin girman da ya ssmu wajen aiki , Dumm ! Yayi , ƙaƙa ankayi ta san an masa ƙarin girma ? Kamar ta san tunanin da yake cikin dariya tace ma sa    Ɗazu na gani a tv , gaskiya ɗan nan ka sha hotuna , anya hasken majigin hoto bai kashe ma karfin gani ba ? Yadda ka ƙware a rawar nan ta ku ta soji ka burgeni ai naso ita ma wannan matar ta ka tana gani ,da ta ga yadda kake shan juyi a fili nasan dole ka burge ta , hahaha Ɗan murmushi yarima yayi yana maida kallon sa ga falmata wacce take gefe a ƙasa riƙe da baby mama , alamun rashin kuzari duk sun bayyana agare ta ,    Fatima miƙo min ɗiyar ki na ga fuskar ta ko kouwa har yau kina mini rowar ta ne ?? Cikin sauri ta girgiza kan ta , "    Hajja miƙa ma sa ita ! Hajja me wurya ta karbi baby ta bashi ,   Ya karbe ta yana tambayar yanayin lafiyar jikin ta a yanzu ? Hajja ta amsa masa da samun tabbatuwar lafiya ga baby mama , ya shagaltu da yiwa ƴar sa wasa daga shi sai falmata da ke rakuɓe daga chan gefe , Hajja tana cikin kitchen tana aikin gyarawa tare da sanya duk wasu kayan abinci a inda suka dace , bata yi aune ba ta ji ƙarar bindigogi da sauti iri iri ya karaɗe falon da ya sa ta yunƙura da gudu tana neman wajen tsira , rashin sanin kan falon ya sa ta dunga cin karo da kujeru ,     Wani mummunan karo ta ci da doguwar kujerar falon da yasa tayi baya tare da sakin ihun da yasa biyamuradi miƙewa a zabari ya taro ta da hannun sa ɗaya , jin mutum a kusa da ita da ƙara kusantowar harbe harben da take ji ya sa ta ƙwaƙumewa a jikin sa ta zagaye dukkanin hannunwan ta biyu zuwa bayan sa , Hajja da ta fito da gudu saboda jin ihun falmata da ƙarar harbe-harben bindiga , sai ta ɗan yi turus tana yawo da ido neman bindigar take , Miƙa mata baby mama yayi ganin yadda take ƙoƙarin sanya kuka saboda ƙaƙƙarfar rungumar da falmata tayi masa ya sa ta firgita , Hajja ta karɓe ta tana cewa ƙarar bindiga nake ji ɗan nan ,  ince dai ba wai yaƙi aka soma ba ?? Bai amsa mata ba illa zaro wayar sa da yayi daga cikin aljihun sa bai duba waye ke ƙiran ba ya katse kiran ,   Hajja ku yi haƙuri sautin ƙiran téléphone ne hakka ba wani abou bane ya kai ga faruwa ba , Au to to , ai cewa nake yaƙin ne ya biyo mu har nan , ! Wucewa tayi da baby mama ɗaki tana neman abin goyo ,! Fatima    Sakar ni haka nan , na faɗi miki ƙarar talfo ne ...    Wayar sa da ta sake ɗaukar ruri ita ta sa falmata ƙara sanya ihu tana sake shigewa jikin sa idan banda ƙyarma babu abunda jikin ta ke yi , Sauri yayi ya ɗaga kiran ganin sunan me ƙiran na sa        princesse Allô ma jolie fille. Ya furta dai-dai lokacin da yake yin baya ya zauna akan kujerar da ya tashi tare da falmata wacce har lokacin riƙe take da shi tsam ta runtse idanun ta , Allo Mon amour ! tu me manques mon amour comment vas-tu aujourd'hui?   Gimbiyar maimouna ta amsa masa cikin salon sautin ta na gogaggun matan da suke tsakiyar ganiyar su , Je vais très bien et tu me manques aussi,      Ya amsa mata yana jin yadda daɗin sautin ta yake ratsa jikin sa ,         Ma princes , Albishirin ka ?    Tace da shi  . Ɗauke da amon murmushin da ya bayyana har a fuskar sa yace  ,    Gorro farare gimbiya ! Ko kassan yanzou jakka ( jakadiya )  ke sanar mouna saƙo ya taho dagga masarautar ku maigirma , ɗauke da gorron tsayar da ranar amren mu , gomma ga wata me kamawa , tabbas sa'a zata tabbata gare ni ranar da anka ɗamra amren mu da kai biyamuradin maraɗawa ! Wani irin daɗi ne marar misaltuwa ya ji yana ratsa zuciyar sa , tabbas zuciyar sa na ƙaunar maimounatu fiye da kowacce ɗiya mace , samun ta kuma nasara ce maigirma saboda a ta suffa da ƙawa tayiwa sauran mata zarra a wajen sa ,     Cikin shauƙi ya sake riƙe wayar sa da kyau yana ɗan bubbuga bayan falmata wacce ta fara dawowa hayyacin ta , da ɗayan hannun nasa , Wannan albishir naki mai girmou ne tauraruwar Agades , votre histoire a fait son chemin dans mon cœur, s’enfonçant dans mon âme. tamkar Falmata ta ji abunda ya faɗi , sai ta ɗago kan ta daga jikin sa , a hankali ta zare jikin ta daga nasa , ta miƙe tana taku sannu-sannu da ƙoƙarin barin falon , zuciyar ta shaƙare da haushin sa , ita shiyasa ta tsani soja , kome na su akwai sumfurin mugunta a ciki bayan haka tayaya sautin ƙiran waya da ta san ƴar ƙara ce mutane ke sawa a wayoyin su amma sai ga shi ta shi wayar ruwan alburusai take har da tashin boma bomai ," Cigaba yayi da hirar sa cikin nishaɗi yana jin yadda albishirin da tayi masa yake ƙara masa kuzari , lalle maimartaba yayi masa attaque par surprise       Fiye da mintoci ishirin suna hirar su sannan suka yi sallama ya aje wayar sa ,        Bankwana yayi da hajja wacce har lokacin tana kitchen goye da mama tana girka musu ɗan abinda zasu ci kafin kwanciyar bacci ,         Har ƙofa ta raka shi tana masa addu'a da godiya     Inda yake sanar da ita gobe zai wuce garin su zai iya kaiwa sati biyu zuwa kwanaki ishirin idan ya tafi saboda haka zuwa goben su masa lissafin abubuwan da zasu iya buƙata baki ɗaya ,     Bayan fitar sa ta kulle ƙofar ta dawo ciki zuciyar ta cike da wasi-wasi akan hirar da ta ji youssouf ɗin na yi da wata wacce bata kai ga sanin wacece ba , sai dai cikin hirar su da mafi yawa da faransanci shi youssouf ɗin yake bada amsa , ta fahimci mafi yawan maganganun nasa na soyayya ne saboda zaman da tayi a ƙasar kamaru , kurtun ɗan sanda ne mijin nata a bariki suka yi rayuwar su dan haka sosai take tsintar wasu kalmomin faransanci duk da dai shekaru ya sa ta manta yaren sosai ! A fahimtar ta youssouf yana da wata mace wacce yake tsanananin so da a kowanne lokaci zata iya cuso kan ta cikin rayuwar sa ta mallake shi wanda hakan yake babbar barazana ga rayuwar auren sa da yarinya falmata miskiniya ,    Hodijan ! Kai tsaye ɗakin da falmata ta shiga nan ta tasamma ,   A zaune ta tarar da falmatan daga ƙasa a bakin ƙofar ɗakin ta takure , Kallon ta tayi ta ji tausayin ta ya tsirga mata , hakkun ta fara hango ƙalubale a rayuwar auren yarinyar da ko fahimtar kalmar auren ma ba ta kai ga yi ba ,   mutuniyar kina zaune anan ne ?? da sauri falmata ta ɗago kan ta ,   Hajja ya tafi ??  Mama tana hannun ki ?    Eh ya tafi ga kuma mama a baya na , taso nan muyi wata magana kin ji ƙawalliye roman jaɓa ! ****** Abuja Nigeria Yakaka ta dage da neman ilmi tun ana koya mata haruffa ,A ,B,C,D , da kuma ا ب ،ت ،ث، sannu sannu ta haddace su tare da iya rubutun su , aka fara haɗa mata jimla , tana koyan rubutun su tare da sanin ma'anar su , ba ƙaramin daɗin koyar da yakaka malama maryam take ji ba saboda wankakkiyar ƙwaƙwalwa me saurin ɗauke abu da yakaka take da ita , A hankali ta fara lura da ƙarancin wayon da yake ga yakaka tare da gidadanci , sai tayi ƙoƙari tana gyara mata duk lokacin da ta ga tayi wani abunda bai kamata ba , tare da yawaita yi mata ƴan nasihu akan duk wasu manya da ƙananun zunubai . Gefe guda lubna na ƙara zage damtse ita a dole sai yakaka ta iya English da arabic ta iya magana da yarukan kamar yadda ta iya , dan haka sai ta tsiri yiwa yakaka magana da English ko Arabic ta daina yawan yi mata magana da hausa koyaushe , ga bangaren yakaka ita ma ƙwarai ƙwarai take jin daɗin haɗuwar ta da malama maryam da ƴaƴan ta , domin sun ja ta a jiki suna kuma gwada mata ƙauna hatta mahaifin su da ba sosai ma suke haɗuwa ba , amma duk lokacin da suka haɗu yana amsa gaisuwar ta faram-faram babu nuna tsangwama , Dan haka gidan su nan ne wajen yinin ta idan babu makaranta , ranakun makarantar ma daga ta baro makarantar gida zata tayi sallah ta ci abinci ta sauya uniform ɗin ta , ta dawo gidan ta kama musu ƴan aikace aikace kafin malama maryam tayi sallah ta ɗan huta , zaman ta da samy baby sai ya ƙaranta , Ranar wata litinin an tashi da hazo sosai tare da sanyi mai tsanani tun safe , zuwa yamma sai hazon ya ƙaru sararin samaniya yayi jawur iska me ƙura tare da tsananin sanyi yana kaɗa jikin al'umma , kusan kowa sauri-sauri yake ya gama abunda yake a titi ya koma gida Bayan tashin su yakaka a makaranta tare suka dawo da malama maryam ita ta wuce gida da zummar yin sallar la'asar ta ci abinci ta sauya kaya ta koma gidan malama maryam wacce ta sake jaddada mata kan lalle fa ta zo su yi darasi kar ganin yanayin garin ya sa ta ƙi zuwa , cikin ladabi ta amsa da    To zan zo Anty ! Da sallama ta tura ƙofar falon samy baby tare da danna kan ta kai tsaye , abunda ta gani ya sa jakar hannun ta saɓulewa zuwa ƙasa ,    Ɗaya daga cikin ƙawayen samy baby ne tare da saurayin ta suke yin masha'ar su nan kan kujerar falon babu kunyar ubangiji ko shakkar za'a iya shigowa agan su haka , Da sauri yakaka ta kawar da ganin ta daga kan su , tare da sunkuyawa ta ɗau jakar ta da sauri ta wuce ɗaki ba tare da ta sake kallon su ba tana jin yadda jikin ta baki ɗaya ya ɗau rawa da tasowar sabon yanayin da take ji cikin illahirin wata jijiyar jikin ta ," A kasalance ta gama kome hatta cin abincin ta da samy baby take ajiye mata shi a ɗakin ta, ta shiryo ta fito falon da fatan son sake ganin su , saboda ganin su na ɗazu da ya tayar mata da wani yanayi cikin jikin ta tare da bijiro mata da guguwar begen yarima da ta ɗan kwanta sakamakon mayar da hankalin ta da tayi kan karatu , sai dai ganin da ta yiwa waɗanan fasiƙan ya sa ta fara tuno da wasu abubuwa masu kamanceceniya da wanda ta ga suna aikatawa , da abunda ya shiga tsakanin ta da bature kam silum , ba ta tarar da su a falon ba , dan haka ta sanya ƙafafu ta bar gidan , tana tafe tana jin ƙewar bature kam silum na sake lulluɓar ta , ko yana ina yanzu ? Wataƙila ma ya manta da ita ! , ruwan hawaye ta ji suna taruwa a idanun ta ,daidai lokacin da take tura babbar ƙofar gidan su malama maryam ta shiga ,    karaf suka ci karo da lubna wacce take ƙoƙarin fitowa daga gidan hannun ta riƙe da wata leda , Yauwa ƙawata Dan Allah zo ki raka ni wancan gidan ummi ta aike ni ,    Tana mata nuni da wani babban gidan da yake chan kusa da ƙarshen layin su ,    Ba musu ta bi bayan ta , lokacin da lubnan take jan hannun ta ,    Saƙo lubna ta kaiwa matar gidan tana bata saƙon suka mata sallama suka yi fitowar su , Sun zo dai-dai tsakiyar harabar babban gidan , yakaka ta ga wani ɗan dogon saurayi ɗan gayu ya sha gaban lubna fuskar sa a marairaice idanun sa fes akan ta ,    Lubna Haba dan Allah ki saurareni , yau wajen watanni bakwai kenan ina bin ki da soyayya ta amma kina min walakanci , dan Allah ki TAIMAKA MIN ki yadda da soyayya ta wallahi ina tsananin son ki ,    Ba tare da lubna ta ɗaga ido ta dube shi ba ta kewaye shi ta wuce tana sake jan hannun yakaka , Charaf ! Ya riƙo hannun ta Lubna Dan Allah ki taimak....   Wani irin ƙara lubna ta sa kamar ya jona mata wuta , ta warce hannun ta da matuƙar ƙarfi cikin abinda bai wuci daƙiƙai ba ta cire hannun ta ta wanke shi da mari , kafin cikin muryar ta da take karkarwar kuka ta tace     Kar ka kuskura ka sake taɓa ni , ni ba ƴar iska karuwa ba ce ,    Kukan da ya zo mata ya sa ta kasa ƙarass zancen ta da gudun gaske ta juya tana barin gidan ,    Yakaka wacce take sakakai a tsaye ta bi shi da kallon tausayi a hankali ta furta kalmar     Kayi hakuri   Gƴaɗa mata kai yayi Cikin sanyin jiki ta juya ta bar shi a wajen ta nufi gida , Tana shiga cikin gidan ta tarar da lubna rungume jikin mamar ta banda kuka babu abunda take , malama maryam sai tambayar ta take me ya same ta ? Me aka mata ? Ta gaza bata amsa ,   Kallo mai bayyana haushi yakaka tayi mata lokacin da take zama a gefen malama maryam , Anty wai fa dan kawai wani mutum ya kama hannun ta yace ta taimaka masa yana son ta shine ta mare shi ta gudo gida tana wannan kukan ,    Ta ƙarasa zancen muryar ta na nuna jin haushin abunda lubna tayi ,     Waye ya kama hannun ta ? Wanne mutum ne , ke lubna ɗago ki dube ni waye ne ya riƙe miki hannu meye tsakanin ku da shi ? Ki faɗa min gaskiya ,    cikin shisshiƙar kuka lubna tace ummi , Mukhtar ne ɗan gidan Alhaji Umar , shine tun watannin baya yake tare ni yana cewa wai yana so na , shine yau ya tare ni a gidan su har ya riƙe min hannu wai na taimake shi yana so na ,     Nan take fushi mai tsanani ya bayyana a fuskar malama maryam , ta shiga yin faɗa meyasa tun ranar farko lubna bata sanar mata ba ? Ita kuma ta faɗawa baban su lubnar ya sami mahaifin yaron anyi musu tsakani ba ,     Faɗa take yiwa lubna tamkar zata doke ta , a karshe ta gargaɗe kan ko kusa ta da shi bata yadda ta sake tsayawa ba kuma zata faɗawa baban su ya sanar da mahaifin yaron su ja kunnen ɗan su , ya fitar harkar ƴar su ,   Sororo ! Yakaka tayi cikin jin mamakin malama maryam menene abun tashin hankali haka ?   Da son kwantar mata da hankali tace ,    Anty ai hannun ta fa kawai ya riƙe , kuma fa cewa yayi ta taimaka masa , wani irin kallo malama maryam tayi mata ,    Yakaka , Namiji baligi ya kama hannun mace baliga haramun ne a musulunci , muddin ba muharamman juna suke ba domin tafarki ne na samar da ZINA a tsakanin mace da namiji  , Zina kuma haramun ce a musulunci, kuma tana daga cikin manyan laifuka wanda ake kira Kaba'ir. Allah ya fada cikin Qur'ani و لا تقرب الزنى Wato kada a kusanci zina. Hikimar fadin hakan shine ba aikata zina kadai ba, aikata abunda zai janyo zinar irinsu rungumar juna , taɓe-taɓen juna da shafe-shafen jikin juna tsakanin namiji da mace dukkansu Allah yayi hani domin hanya ce ta kusanta kai ga zina , cikin sanyin murya yakaka tace Anty menene ZINA  ?? Zina ita ce Saduwa a tsakanin namiji da mace ,( ina nufin mace da namiji su kasance cikin abun rufuwa ɗaya jikin su na cikin na juna , azzakarin namiji yana cikin farjin mace ) ba tare da hukuncin aure ya shiga tsakanin su ba , duk mace da namijin da suka yi tarayya irin haka ba tare da an ɗaura musu aure kamar yadda addinin musulunci ya koyar ba to babu shakka sun aikata zina , kamar yadda na faɗa miki ita zina tana cikin manyan laifukan da Allah yayi hani da su sannan kuma ya tanadi hukunci ga duk waɗanda suka aikata ta , Hukuncin Zina a shari'ance ,  ita zina ba'a tabbatar wa da mutum ita dole sai da hujjoji, hujjoji guda biyu ne ko dai mutum ya yarda da kanshi ya aikata , ko kuma mutane huɗu su ganshi turmi da taɓarya a wannan hali ne ake tabbatar da zina, Amma ko mutune uku ne suka ce sun ganshi turmi da taɓarya sai ɗaya yace shi dai ya gansu a tube suna shafe shafe to baza a karbi shaidun su ba, za'ai musu bulalar ƙazafi tamanin tamanin , Amma idan shaidu sun kammala ko mutum ya amsa da bakin sa yayi zina Hukuncin sa a shari'ance shine bulala ɗari ga waɗanda basu taba aure ba. Kamar Yadda Allah ya faɗa" الزانية والزانى فاجلدا كل واحد منهما مأة جلدة، ولا تأخذكم بهما رأفة فى دين الله إن كنتم تؤمنون بالله واليوم الآخر. Wato mazinaci da mazinaciya ayi wa kowanne su bulala ɗari, kada tausayi ya kama masu dukan idan har sun kasance masu imani da Allah da ranar lahira. Sai wanda yayi aure akwai hadisin da yace duk mai aure ko wanda ya taɓa aure idan ya taɓa zina za'a jefe shi, amma sai idan shine da kanshi yazo yace yayi zina yana so a jefe shi, amma idan bai yadda a jefe shi ba ba za'ayi mishi dole ba za'a barshi ne. Wani irin tsoro da tashin hankali me tsanani ne ya dirar mata , cikin wata irin muryar da ke bayyana tsantsar firgicin da ruhin ta ke ciki , tace    Anty ko da mutum taimako yayi , Malama maryam cikin tsanaki tace ban fahimce ki ba yakaka wanne irin taimako ne yake zuwa ta hanyar aikata zina ?? Anty ina nufin ko shi namijin cewa yayi mace ta taimaka masa , sai ita ma ta taimaka masa , suka yi , shikenan tayi zina ?? Su dukan su sun aikata zina , saboda babu biyayya ko temakekeniya tsakanin bayin Allah wajen saɓa masa , su dukkanin su basu da hujjar kare kan su , suyi gaggawar tuba ga ubangiji domin zina babbar musiba ce , Sannan kuma yakaka ai duk namijin da zai cewa mace ta taimaka masa ta bashi kan ta suyi zina , ai wannan babban maƙiyi ne a gare ta , bata da maƙiyi sama da shi , mugu ne kuma macuci domin na farko zai ɓata tsakanin ta da ubangiji , yasa ta aikata abunda Allah zai yi fushi da ita , da zai hana ta samun ganin Alkhairi da dacewa cikin rayuwar ta duniya da lahira har sai idan ta tuba , Na biyu duk ranar da mutane suka san me suke aikatawa, mutanen kirki zasu guje ta , za'a dunga mata kallon fasiƙa, mazinaciya ƴar iska , karuwa . Na uku idan ta hanyar zina da suka aikata ta samu ciki ta haihu , abun da ta haifa idan ya girma shi ma da kan sa zai tsane ta , ƙimar ta zata zube a idanun abunda ta haifa , saboda ta zamto sanadin da mutane zasu dunga ƙyamatar sa da ganin sa wani mutum da aka samar da shi ta haramtatciyar hanya , Bayan haka illolin zina suna da yawa , daga ciki akwai ɗaukar munanan cututtuka da zasu iya kai me su ga mutuwa , A ƙarshe namijin da duk zai yi zina da mace abu ne me wuya ya aure ta , ko da ya aure ta kuma bazai taɓa ganin ƙimar ta da mutuncin ta ba , sannan ƙanƙanin kuskure zai iya haifar da zargi a tsakanin su da zai lalata musu aure , Kuma duk macen da tayi zina kafin tayi aure bata da wata martaba a idanun duk wani namijin da zai zo ya aure daga baya saboda ta rasa ƙima da mutuncin ta na ƴa mace tunda tayi zina . Ki gujewa abunda duk zai kai ki ga aikata ZINA yakaka cikin ta akwai tarin masifu kin ji ko ?? Bata amsa ba illa miƙewar da tayi bata tsaya ba ta taka da gudun gaske tana barin gidan ba ta ko tsaya ta sanya takalman ta ba bare ta saurari ƙiran da malama maryam take mata , gudu take bata ko dub Inda take jefa ƙafar ta ,    Da ƙarfi ta tura ƙofar ɗakin tana shiga ta zuɓe a tsakiyar ɗakin tana sakin wani irin kuka marar sauti da yake tuƙowa daga ƙasan ruhin ta ,    Cikin wata irin murya ta fisgo kalmar ,    ALLAH NA TUBA , NA TUBA ALLAH , BAZAN SAKE BA ,ALLAH NA TUBA KA YAFE MIN ,   Kuka take tana maimaita kalmomin nan jikin ta har tsuma yake , Ashe haka ne girman laifin da ta aikata batare da ta sani ba ? Ashe ita ɗin me tarin zunubi ce ? Ashe baza ta samu wani alkhairi ba arayuwar ta tunda tayi zina , Ta jima a zaune a wajen tana kuka har duhun dare ya shigo , zuciyar ta ta tsorata iyaka , neman yadda zata yi Allah ya yafe mata take yi , sai dai bata san yadda zata yi Allah ya karbi tuban ta ba , ji take kamar zata mutu , Tashi ta sake yi tana gama hanya saboda kukan da ta ɗauki lokaci tana yi yasa kan ta sarawa tare da fara jin jiri , tana gama hanya ta fito , bata ko dubi ɗakin samy baɓy da kiɗa ke tasowa ta cikin sa alamun da ke nuna ta dawo gidan ba , ta sake fita , hanyar gidan malama maryam ta sake  ɗauka ,   tana so ta san yadda zata yi Allah ya yafe mata , tana so ta san yadda zata yi ta gyara kuskuren ta , a falo ta tarar da malama maryam tare da iyalan ta suna cin abincin su na dare ,    Babu sallama ta rakaɓe daga bakin ƙofar gami da sakin kuka me ciwo , hankali tashe malama maryam ta tsame hannun ta daga abincin da suke ci ta miƙe , ta zo ta kama yakaka ,     Tambayar ta take lafiya ?meye ya same ta ? Ko wani abu ya samu antyn ta ? Daman yanzu take so idan ta gama cin abinci lubna ta raka ta gidan nasu ta duba ta domin ɗazu ta fita bata cikin nutsuwar ta yanzu kuma ta dawo tana kuka , shin menene yake damun ta ??      Cikin muryar ta da kuka ya fara disarwa , tace nayi ZINA malama maryam , ki taimake ni ki faɗa min yadda zan yi Allah ya yafe min , ban sani ba malama maryam wallahi ban sani ba ,   Ta shi , ta shi mu shiga ɗaki ki nutsu ki min bayani yadda zan fahimce ki ,    Ta kama hannun ta zuwa ɗaki ta zaunar ta bakin gado , ina sauraran ki me kike son faɗa min yakaka ? Tiryan tiryan , yakaka ta fara bada labarin tun daga farkon haɗuwar ta da yarima har yanayin yadda abubuwa suka kasance har zuwa yadda alaƙar ta da samy baby da yadda ta yaudare ta ta zo da ita garin  abuja ta baro ɗanyar jaririyar ta tare da makauniyar ƙanwar ta,  bata idasa ba malama maryam ta katse ta , Kin yi kuskure yakaka , kin yi kuskure , kin yi kuskure ,! Kaicho       wani irin tausayi chakuɗe da bacin rai take ji cikin ran ta , tamkar wata makusanciya a gareta ce ta aikata abubuwan da yakaka ta aikata , tun farkon fara koyar da yarinyar ta fahimcin tana da raunin sani sosai da sosai game da addini , kusan ma bata san kome ba , shiyasa ta ɗaura aniyar ganin ta kawo sauyi ta fidda ta daga duhun jahilci , cikin rashin sanin ta ashe jahilci tare da rashin wayon yarinyar har ya kai haka ( Bata san menene zina ba ) ? Ta yadda aka yi amfani da jihilcin aka cutar da ita cuta mai tsanani irin haka ? Kukan da yakaka take ya tsansnta ganin shirun malama falmata ya ɗau lokaci tare da bayyanuwar matsanancin tashin hankali bisa fuskar ta ,   ALLAH zai yafe miki yakaka , muddin kika nemi yafiyar sa tare da niyyar baza ki sake komawa ga aikata saɓo irin wannan ba , ALLAH me yawan gafara ne ga bayin sa , Duk da cewa akwai bayanai daga malamai game da mutumin da ya aikata saɓon Allah alhalin bai san cewa sabon nan me girma bane da zai iya kai me shi ga shiga wuta ,ko kuwa bai ma san saɓo bane baki ɗaya, akwai hukunce hukunce , hukunci na farko shine , Shi JAHILCI ba'a uzuri da shi, sai dai cikin wannan hukuncin akwai bayanai da suke nuna akan karbi uzurin JAHILI , idan ya kasance gurin da ka tashi babu addini , babu malamai masu koyarwa ,ko kuwa an hana ka damar fita neman ilmin kuma ba'a koyar da kai ba a gida ,  to za'a iya yi maka uzuri da wannan , amma idan gurin da kake akwai addini akwai malumma , sai kaƙi fita ka nemi ilmi kasan hukunce hukuncen addini kayi zaman ka cikin jahilci to wannan baka da uzuri a addini , jahilcin ka ba uzuri bane , to amma idan ka rasa damar samun ilmi ne , akwai hadisin manzon Allah sallalahu alaihi wa sallam da yake cewa :      Allah ya ƙetarar da Al'umma ta abu uku , ma'ana ya yi musu afuwa akan abu uku , na farko shine mutum yayi abu cikin rashin sani , na biyu mutumin da ya aikata wani kuskure akan mantuwa , sai na uku wanda aka tilasta ma sa aikata saɓo, ! To idan aka yi duba ga wannan hadisin za'a yiwa mutumin da duk ya aikata wani saɓo cikin rashin sani , uziri a sassauta masa , sannan shi kuma yayi tuba zuwa ga Allah , tsarkakaken tuba , Manzon Allah yana cewa : duk wanda yayi tuba na gaskiya to zai kasance kamar bai taɓa aikata wannan Zunubin ba , amma wanda yake tuba alhali yana komawa ga aikata zunubin sa to tamkar yana yiwa Allah izgili ne . kiyi Tuba na gaskiya yakaka tare da niyyar baza ki sake kusanta kan ki ga aikata ZINA ba a rayuwar ki , Allah zai yafe miki ya wanke ki a idanun Al'umma domin Laifin shi kika yiwa , Sannan , ki tashi ki nemi ilmi ki kuma yi aiki da shi idan dama ta samu gare ki kome ƙanƙantar sa ki koyar da ilmin da yake gare ki domin sauran Al'umma su amfana , shiriya ta zo miki hasken ilmi ya zo miki ki sa hannu biyu ki karɓe su ƙwarai akwai falala tare da samun dacewa a cikin su , ki manta da rayuwar baya ki himmantu wajen neman gafarar ubangiji akan saɓon da kika wanzu kina aikatawa , da fatan kin fahimce ni ?? bata amsa ba illa hannu da ta kai ta rungume malama maryam , idanun ta na zubar ƙwallar da ita kaɗai ta san dalilin sauƙar su a daidai wannan lokacin Godiya ta dunga jerowa malama maryam har lokacin da ta sanya ƙafar ta tana barin gidan lokacin dare ya fara shiga karfe goma saura , kan titi babu kowa garin ya sake ɗaukar sanyi , a hankali take tafe iska yana ɗaga hijabin ta , tayi zurfi cikin tunani , daki-daki take tuno kome da ya dunga faruwa a rayuwar su ita da ƙanwar ta , tana so ta zargi iyayen su akan killace su a gida da suka yi suka hana su neman ilmi , sai dai so irin na tsakanin ɗa da iyayen sa ya mata dabaibaiyi yaƙi bata dama , ji take suna da wata hujjar su , babu shakka akwai dalili , tunanin falmata da baby mama yayi mata dirar mikiya , wata irin kunyar falmata ta ji tana nuƙurƙusar ta , yaya zata Ji ranar da duk ta san irin kuskuren da tayi har ta samar da baby mama ta gudu ta bar mata ita ? Wataƙila daga ranar zata fara tsanar ta , tsoro take ji tsoron girma ya zowa baby mama ta samu sani akan irin ta hanyar da aka samar da ita , ? Me zata cewa waɗannan bayin Allah biyu ?? Lalle wajibi ne a gare ta ta nemi ilmin addini ko domin ta samun ƙarfin guiwar da zata iya fuskantar su tare da tarin hujjoji da bayanan da addinin ya tanadar domin ta gamsar da su ta kuma wanke kan ta a idanun su su san cewa ta aikata kome ne cikin DUHUN JAHILCI ,! Ko zasu fahimce ta ? Ko falmata zata yadda ta cigaba da riƙe ta a matsayin ƴar uwa masoyiya ? Ko baby mama zata yadda da ita a matsayin uwa ?? Yaushe wannan ranar zata zo ? Zata zo nan kurkusa , ko sai bayan shuɗewar tsawon wani lokaci ? Abun da ta riga ta sani muddin su na raye wannan ranar zata zo , YARIMAN MARAƊI , Zuciyar ta ta auno mata da sunan sa da kome da ya wakana cikin rayuwar ta a wannan gaɓar shine sanadi , bata gan shi ko kusa tare da duhun jahilci makamancin nata ba , kome da shi yayi mata yayi ne cikin ilmin sa ,da sanin sa ya aikata Zina da ita , zuciyar ta take ji tana wani irin buɗawa da sabon yanayin da yake shigar ta akan sa da sabon matsayin da ya kamata ta ajiye shi tun farko a ran ta , Tunowa ta fara yi filla filla da farkon haɗuwar su har zuwa ranar ƙarshe da ya kore ta daga motar sa a tsakiyar titi  tana kuka , yayi tafiyar sa ya bar ta har yau bai sake waiwaiyar ta ba , tabbas shi macuci ne azzalumi agare ta bai chanchanta da samun soyayyar ta ba ko kaɗan , bai taɓa son ta ba , kawai amfani yayi da jahilcin ta ya ribaci gangar jikin ta ya yasar da ita tare da cikin da yayi mata , wani irin yanayi mai ƙarfi da kaifi ta ji yana keta zuciyar ta a game da shi , hannun ta ta kai ta tattaro bakin hijabin ta ta riƙe tare da cije gefen leɓen ta na ƙasa da ya zo daidai da zubowar hawayen ta da yake nuni da mummunan ƘULLACIN da tayi masa .... !!!!!! [9/3, 10:13 PM] +234 806 122 1116: Fikrah writers association MAFARI ( Hargitsin Rayuwa ) umm'muaz 31 Ba ƙaramin kaɗuwa Youssouf ya yi ba lokacin da Maimartaba yake shaida masa zancen auren sa da Siyama , da har an riga an miƙa dukiyar auren ta ga mahaifin ta dake niamey , za'a yi ɗaurin auren sa da ƴan matan duk biyu a rana guda kamar yadda ya buƙata , Ya jima a zaune gaban Maimartaba yana jin yadda zuciyar sa take cunkushewa da tarin takaici , Ba tun yau ba ya gama lura da take-taken yarinyar , shi yasa sam baya sakar mata fuska ashe bai sani ba har tayi girman da zata iya yin tsaurin ido irin haka a matsayin ta na mace ta doshi iyayen sa da buƙatar son a haɗa su aure ? Babu shakka zata ɗanɗani kuɗar ta a hannun sa , sai tayi danasanin wannan mummunan shisshigi da tayi ta kutso kan ta cikin rayuwar sa da take a hargitse a halin yanzu , Ganin shirun sa ya tsawaita ba tare da ya amsa da amincewar auren ba , ya sa me maimartaba yin gyaran murya   Da fatan ba zaka bijirewa oumarnin mu ba ? Bisa ga wannan haɗi da munka yi na amre tsakanin ka da ƴar ouwar ka , saboda ba muyi haka ba face sai da munka hango tarin alkhaire tare da dacewa sannan munka so ƙulla igiyar amre a tsakankanin ku , wannan ɗiya ɗiyar ƴar uwa ta ce , kai ma kuma ƴar ouwa take gare ka , ina yi maka oumarni ka karɓi amren nan da hannu biyu da ikon Allah gaba kai zaka yi farin ciki . Kalmar 'Umarni, ta daƙile dukkanin wani yunƙuri da zai iya yi , domin shi ɗin me yawan biyayya ne ga iyayen sa , haɗi da sanin da yayi a yanzu shi me tarin laifuka ne , wanda yake neman wata kafa ko yaya ne da zai iya faranta ran iyayen sa ta dalilin ta, ko domin su iya masa uzuri a duk ranar da laifukan sa suka bayyana a gare su , su duba irin faranta mu su da yayi su sassauta masa hukunci , Cikin harhaɗa kalmomin da suke suɓcewa daga harshen sa saboda kaifin su da yake iya ji ya furta , Na Amince , Allah shi ƙara girma da ɗaukaka . Da murmushi bisa fuskar sa yace Madallah da kai , Allah shi maka Albarka , Ya Albarkaci zuri'ar ka , Allah shi yi katanga tsakanin ka da miƙiya , kana iya tafiya ka fara shiri doumin nan da sati biyu da ranar tayi dai-dai da gomma ga watan gobe ake ɗaurin amre . Godiya yayi ya miƙe yana barin shigifar sarki , kai tsaye gidan da zai tarar da Tafeeda ya nufa , Cikin sa'a ya same shi dawowar sa kenan daga aiki da sanyin la'asar , Babu walwala a fuskar sa ya samu wajen zama bisa kujerun shan iska ,   Ɗan ouwa ka kuwa san me ke shirin farouwa gare ni ? Maida ganin sa yayi kan sa , bayan ya miƙa masa sassanyan lemun da ya tsiyayo masa a kofin gilashi , Sanar da ni ɗan ouwa Wai amren mataye biyu a rana gouda , kuma amre tare da yarinyar nan siyama da ko ƙamnar duban ta bana yi , shin baka yi tounanin akwai wani dalili da ya sa maimartaba haɗa min amren mataye biyu a rana gouda ba ?     Ɗan guntun murmushi tafeeda yayi Banda abun ka Yarima shin amren mataye biyu a rana gouda ba gata bane ?    Ita siyama ai duk inda ake neman macen amre ta zarta ,   Maimartaba bashi da sani kan kome wataƙila hasashe ne yayi irin nasu na manya ya sanya shi yi maka gatan amra maka mataye biyu a rana gouda , Juyar da kan sa gefe yayi yana jin yadda ran sa ke sake ɓaci , kan batun auren , ga kuma ya lura Tafeeda ba shi da niyyar taya shi jimami , shi ina zai kai mata har uku a shekarun nan nasa ??     Kurɓar lemun sa tafeeda yake yi yana satar kallon youssouf da yayi tagumi hannu biyu ya nisa cikin tunani ,    So yake ya masa tambaya game da al'amuran sa na ƙasar nigeria , ɗiyar sa da take can , ƙaƙa ya ƙarƙare da barin ta a chan ? Hannun wa ya baro ta ? Sai dai rashin son tuno masa da ita ya sanya shi haɗiye tambayoyin sa , ga zaton sa Biyamuradi yayi amfani da shawarwarin sa , ya baro duk wasu kuskuren da ya aikata a inda ya aikata su ! Farin cikin da Siyama ta tsinci kan ta cikin sa bai misaltuwa , domin duk wani da ke mu'amala ta kusa ko ta nesa da ita zai iya shaida farin cikin tare da walwalar da ke tare da ita , da ɗai bata taɓa farin ciki me yawan haka ba cikin rayuwar ta ,    Ƙulluwar aure a tsakanin ta da Youssouf wani abu ne da tayi shekaru tana mafarkin sa a bacci ko a farke , bata taɓa zaton zata samu damar mallaƙar sa a matsayin miji a sauƙaƙe haka ba , a kuma daidai lokacin da take zaton ya sulluɓe mata zai zama malakin wata ba ita ba , duk tunanin ta na bata sai wani nisan shekaru wataƙila idan da rabo suyi aure , ga haɓakar farin cikin ta ashe tabbatuwar mafarkin ta zuwa gaske yana kurkusa , ashe tare zasu mallake shi ita da wacce take tunanin ta fita sa'a , ashe sa'ar na gare ne su biyu ,? Bata ji ko ɗar ba akan sanin da tayi auren su auren haɗin iyaye ne , tare da sanin da take da shi akan irin tsanar da shi yake gwada mata , ta ji ta gani ta amince ta kuma shirya yin zaman aure da shi da gasken gaske , cikin kowanne irin hali , tana jin son da ita take masa zai ishe su rayuwa ita da shi ,    Soyayyar sa ga gimbiya maimouna bata razana ta , illa kishi da ke nuƙurƙusa ran ta , dan haka ta sha alwashin ko da ƙaƙa , sai sun raba soyayyar youssouf biyu ita da maimouna kamar yadda zasu mallake shi a matsayin miji su biyu a lokaci guda , idan ya so ita na ta kason soyayyar idan ya so ya zubda a rariya , bata da damuwa son da take yi masa ya ishe su , . Shiri take ka'in da na'in ubbo tana taya ta haiƙan , gefe guda hajiya umma na bada ta ta gudummawar a matsayin siyama na ɗiya a gare ta , ɗiyar da ta goya tayi rainon ta tun tana tsumman goyo , Lokacin da gnala take sanar da gimbiya maimuna dangantakar dake tsakanin youssouf da siyama har ma da zantukan da ta ji siyama na tattaunawa da  ubbo , bata wani ɗau batun da muhimmanci ba , saboda wasu dalilai nata da take ganin ko da ace zai aure su su biyun ita bata jin hakan zai dame ta , burin ta ɗaya tal , shine ta samu nasarar aiwatar da ƙudurin da zai sa ta aure shi . Dan haka ko da yake kame-kamen sanar da ita batun auren sa da siyamar yana bin ta da kalaman rarrashi , kwantar da murya tayi ta dunga zuba masa sassanyan rikicin da ya sake ɗaga darajar ta a idanun sa tare da sake dilmiyar da shi cikin ƙaunar ta ,      Ya dunga jin yayi sa'ar samun nutsattsiyar mace kuma me haƙuri, wacce mace ce a zamanin yanzu da za'a yiwa kishiya gab da lokacin auren ta , a kuma haɗa su aure rana guda , ba'a yi danbarwa da ita ba ? Ƙwarai ƙwarai maimouna ta ƙara ƙima a idanun sa , Samun haɗin kan ta farad ɗaya ya lafa guguwar ƙin auren a cikin ran sa , sai ya samu nutsuwar fuskantar shirye-shiryen auren tare da cigaba da zarya wajen sabon gurin aikin sa da aka tura shi Dosso , inda zai zama shugaban soji na baki ɗayan yankin na jahar Dosso , Tafkeken gida aka mallaka masa tare da motocin hawa biyu , ƙari da tarin hadimai sojoji tun daga kan masu gadi , direba , har zuwa kan me girki . Tsakanin jahar Maraɗi da jahar Dosso babu tazara me yawa , dan haka lokacin da yake da samun tabbacin wajen zama a dosso , sai yayi niyyar bayan bikin su , zai dawo da gimbiya maimouna nan gidan sa na dosso , kusa da shi , ita kuwa siyama ta cigaba da zama can a maraɗi , tunda ita ta zaɓi auren cikin gida sai ta samu matabbata a cikin gidan , ! Sai dai yana sanar da hajiya umma niyyar sa , a take ya ga sauyin fuskar ta ,      Abu guda ta ce da shi . Kome tsanani kayi ƙoƙarin kwatanta adalci tsakankanin matayen da Allah ya baka amanar riƙon amren su , kar ka kuskura ka karkata ga ɗaya daga cikin su , saboda gujewa fushin Allah da azabar sa ka kiyaye , siyama da maimouna duk su biyun matan amren ka ne . ***** Tun farkon satin aka fara gudanar da shagulgula da wasannin daga bangaren masarautar maraɗi har da ta Agades wanda suke da tarin wasannani da al'adun gargajiya fiye da na maraɗi , haɗi da shiri sosai da suka yi na bikin kasantuwar kowa ya san gimbiya maimouna ɗiyar gata ce ta sosai , Har zuwa yau da take ranar sakun lalle ga amare , gobe juma'a za'a ɗaura auren Kamar yadda al'adar masarautar maraɗi take , duk lokacin da za'a yi sakun lalle ba'a yi a cikin masarauta , can tsibirin maraɗi ake tafiya da amayar ,"wani ƙaramin gari ne da yake ƙarƙashin jahar maraɗi da ake ƙiran sa tsibiri bashi da nisa sosai da ainahin cikin garin maraɗi , Gidan sarkin tsibirin nan ake sakun lallen a cikin gidan akwai wata mace da ake ƙira ,inna , wacce sunan sarautar ta ce ,inna ɗin ," ita take sakun lalle ga amaren da duk za'a shigar ko za'a fitar daga masarautar maraɗi, Karfe ɗaya na rana gimbiya maimouna tare da ƙanwar mahaifiyar ta da ƙanwar mahaifin ta da matar maimartaba sarkin agades ta biyu tare da wasu daga cikin matan ƴan uwa na ƙurƙusa tare da rakiyar amintattun hadiman ta mata biyu da bayu maza uku  sai kuma ƙaramar jakaɗiyar agades,  jirgin su ya iso tashar jirgin sama na maraɗi daga agades ,inda nan take motocin da suke jiran su domin kai su tsibiri suka ɗauke su kai tsaye zuwa tsibirin maradi , Tarɓa me cike da girmamawa aka yi musu , inda suka tarar da gidan cike da manyan mata masu sarauta na kurkusa da fada cikin su har da manyan yayun biyamuradi ,"Ammi da Dada da Asma'u da ake ƙira ma'u ƴar wajen hajiya mama ta farko . ," da kuma ƙaramar jakadiya . Tsakanin su bai cika awanni biyu ba siyama ta iso ƙarƙashin rakiyar ƙannen maimartaba sarkin maraɗi su biyu tare da hajiya mama da ubbo sai kuma ƙannen baban ta su biyu , Ta ko'ina buɗa da ƙirari ne yake tashi saboda makaɗa da maroƙa da suka cika faɗar sarkin tsibiri duk da cewa an dakatar da su daga shiga cikin gidan inda aka fara shirin sakun lallen amaren       Shimfiɗa ce aka yi da manyan jajayen dardumai , a tsakiyar babban ɗakin , inda aka ajiye babban tum-tum na zama a tsakiyar shimfiɗar , Inna tayi umarni da a shigo da siyama za'a sanya ta a lalle , Ko kafin bangaren gimbiya maimouna su ce kome , hajiya mama ta yunƙuro ,   Wacce siyama kouwa ? Ai ita maimouna ita ce matar farko dan haka ita za'a fara sanyawa ga lalle ko kouwa ?   Hakka zance yake ranki ya dade uwagijiya ta ,   cewar ƙaramar jakadiyar Maraɗi Aiyuriyuriyyyy ayuririyyyyyy ayyuririyyyy !! Wata zazzaƙar guɗa ta fito daga hancin jakaɗiyar agades , saboda jin babban matsayin da uwargiyar su ta samu ,   Taka a sannou-sannou ƴar sarki jikar sarki , matar yarima ɗan sarki surikar sarki , gaban ki salama bayan ki lafiya  farar macce fitila gida , tauraruowar ki me ƙarfi ce wacce hasken ta ya tarwatsa ya zagaya nahiya tun dagga birnin agades har yankin maraɗi , wouce gabba kin yiwa sauran mata zarra , kin yi gado ba haye kika yi ba mahaifiyar ki ai ita shugaba ta matayen agades ,     A hankali ta sanya kan ta cikin ɗakin tana jin yadda ginshiri irin na sarauta yake sanya ta ƙasaita da jin faɗi. Bayan shigar ta guda daga bangaren mahaifin ta tare da guda daga bangaren mahaifiyar ta suka rufa mata baya , ubbo ta yunƙura zata shiga hajiya mama ta dakatar da ita tare da yiwa ma'u umarni da ta bisu kamar yadda al'adar take mutum ɗaya daga bangaren dangin miji ke shiga ɗakin sakun lallen . Bayan zaman gimbiya maimouna inna ta janye hular alkƴabbar dake bisa kan ta , baƙin gashin ta da ya sha gyara ya bayyana , inna ta sanya wata ƴar kyakkyawar kibiyar kitso ta raba gashin biyu hagu da dama , Matar da take waziriyar inna ta miƙo mata wani ƙoƙo cike fal da madara sanuwa/nono , ta karkata ƙoƙon a sannu sannu ta fara zuba madarar a daidai tsakiyar tsagun , A hankali kakkauran nonon ya fara kwaranya , bisa tsagun kafin ya saki layi ya tarwatse a gaba ɗayan cikin gashin maimakon ya bi kan hanyar da aka masa ƙaɗai , Nan take inna da waziriyar ta suka haɗa ido suna masu gƴaɗa kai a hankali , yayin da fuskar ma'u ta sauya tana bayyana ɓacin rai a sarari , har aka gama zuba nono nan haka yayi faca-faca akan fuska da jikin kayan gimbiya maimouna , A fusace ma'u ta juya ta fita daga ɗakin gefen mahaifiyar ta ta je ta tsugunna ta mata raɗa , nan take fuskar hajiya mama ya bayyana wani sirrantatcen murmushi , kafin tayi gyran murya tayi wa jakadiya alama da ido , Nan take jeka ta karkace kai ta rangaɗa ƙaƙƙarfar guɗa da ta sanya , mutanen agades samun kwanciyar hankali musamman innonin gimbiya maimouna da duk suka sha jinin jikin su , kan shirun da suka ji daga ɗakin ko dai ƴar ta su tayi kuskure ne cikin rayuwar ta ? Amma jin buɗa daga bakin jekadiyar maraɗi ya sa hankalun su ya kwanta yayin da tasu jakadiyar ma ta karkace kai ta dunga sakin zaƙaƙan buɗoɗi ,   Bayu mata biyu suka jawo wata ɗirkekiyar tunkiya fara sol suka ɗanka ta ga hannun matar sarkin agades ,    Tunkiyar gimbiya maimouna ce ta sakun lalle , nan take bayun agades suka kama igiyar tunkiyar suka riƙe gam . Ma'u ta koma ɗakin ƙarƙashin umarnin hajiya mama ta sanya farin kyalen ta share fuskar gimbiya maimouna gami da jan hular alkyabbar ta ta rufa mata akan ta , Suka fito daga ɗakin , Bayan an sauya shinfiɗa da wajen zama aka yi umarni a shiga da siyama , Ƙanwar mahaifin ta ɗaya tare da hajiya mama sai kuma ubbo su ne suka shiga da ita ta zauna akan tum-tum Inna ta tsaga gashin ta , ta karbi ƙoƙon madarar ta shiga tsiyayo mata shi daga tsakiyar kan ta sannu sannu ya shiga bin layin yana gangarawa har zuwa kan siririn karan hancin ta yana ɗiga a gaban rigar ta , har nono ya ƙare bai karkace hanya ba , Wata ƙarƙarfa guɗa ce ta taso daga hancin inna da tayi amsa kuwwa har fada da nan take makaɗa suka ƙara ƙarfin kiɗan su da ƙirari , Daga waje ma bayun masarautar maraɗi suka dunga sakin buɗa ba ƙaƙƙautawa , Zuciyar hajiya mama tayi bakikkirin lokacin da ubbo ta sunkuya ta ɗau farin kƴallen tana gogewa siyamar madarar fuskar ta idanun su suka gauraye cikin na juna sassanyar ƙaunar da take tsakanin su tayi tasiri idanun siyama suka ciko da ƙwallar murnar ganin wannan ranar me cike da ɗinbin tarihi a wajen ta , a hankali ubbo ta kai hannun ta duk biyu ta rungumo siyamar zuwa jikin ta , a hankali ta raɗa mata a kunne    Madallah da ke ƙauna ta ɗiyar kirki , me daraja ,Madallah da ke mace tagari abar alfaharin iyayen ta da mijin auren ta ! Ko kusa ran hajiya mama bai yi daɗi ba da cikar budurci da alamu suka bayyana ga siyamar kamar yadda al'adar daman take nuni ne da macen da take cikakkiyar budurwa ita ce wacce nonon ke bin dai-dai tsagun layin ba tare da ya karkace ba , ta so ƙwarai ace an samu matsala irin wacce aka samu ga gimbiya maimouna , domin tayi amfani da damar wajen hana yiwuwar auren siyama da youssouf wanda ta ji zancen sama ta ka babu zaton ta babu tsammani , kuma a zahiri bata ƙaunar duk wani abu na alkhairi ya raɓi youssouf , Sannan irin tashin hankalin da mommoudu ya shiga da jin zancen haɗin amre tsakanin youssouf da siyama , alhalin shi zuciyar sa ta rayu tsawon lokaci ɗauke da dakon soyayyar siyamar , meyasa kome na cigaba da samun nasarar rayuwa yana ga youssouf ba shi ba ? Meyasa maimartaba ya tattara duk wasu gata da kulawa ya bada ga youssouf alhalin ga shi , shine kuma ƙarami ? ******* Biki aka yi na bajinta da gata , irin wanda ba'a taɓa yin makamamcin sa ba a tsakanin jahohin biyu , aka yi biki aka gama lafiya lau amare sun ka tare a gidajen su da suke cikin da'ira guda sai dai kowaccen su tana sashin ta yayin da sashin biyamuradi yake tsakiyar nasu , gini ne guda uku a tsaye , Daren ranar lahaɗi da aka yi wuni aka watse shine daren da farkon sa yake zaƙi ga youssouf kafin zuwan tsakiyar sa da kome ya rikiɗe ya kuma sauya ya birkice ya hautsine masa , ya sanya shi shiga ruɗani , nadama bakin ciki tare da tarin tsoro , Maimouna ita ce macen da ya ɗau aniyar kwada mata ƙauna da soyayya irin wacce yake da burin nunawa ga matar auren sa , hakan kuma ya fara gwada mata a tun farkon daren da yake jin tamkar ya haɗiye ta dan so ko kuwa ya buɗe cikin ƙirjin sa ya cusa ta , sai juyi da ita yake yi yana lallaɓa ta daki-daki tamkar ƙwai , kafin kome ya kankama , zuwa lokacin da zai fahimci bara gurbin ƙwan da ya ɗaukowa kan sa ya kuma ta'alaka soyayyar sa akan ta , har ma ya sallama mata duk wani so gami da yadda da ya mallaka , Ashe yayi kuskure ne , shin ashe ta riga ta so wanin sa kafin shi ? Har ma ta mallaka masa abu mafi daraja agare ta wato gangar jikin ta ? Ashe ita ɗin ta ha'ince shi ne ? Shin ko dai shine ya ha'inci kan sa ? Shin ko dai ayar Ubangiji ce ke tabbata akan sa ? Idan kayi zina da matar wani ? Idan kayi zina da ƴar wani ?  Idan kayi zina da ƙanwar wani ?? Uwar wani ?? Tunanin hakan ya tsorata shi tsoro me tsanani , da ya hana tasirin fushin sa bayyana har ya nuna shi ga gimbiya maimouna da ta cigaba da yi masa lamɓo da nuna masa salo salo na gogaggun mata har da ƴan ƙananun koke koken ta , ita ciwo take ji , Sai yayi wani zugum kamar soko ya sanya mata ido , ah to shi zata yi wa bariki ?? Ai ya san me ake nufi da budurci , " amma tunaninikan da suke bijiro masa da shuɗaɗɗen laifin sa suke barazana ga nutsuwar sa saboda zuwan dodo-dodo da suke masa suna sake maimaita kan su tare da bada fassara akan halin da ya riski matar sa a ciki , Hannun sa ya kai da ƙarfi ya jawo ta ya jefa kan ta kan ƙirjin sa yana jin yadda iskancin kukan da take yana sake dagula masa lissafi , Ɗan Allah ki min shiru   Yace da ita , a tsawace Da yake daman kukan gulma ne sai tayi luf kafin gajiyar biki tare da gajiyar farkon daren su danne ta bacci me matuƙar ƙarfi da daɗi ya silalo ya chafke ta , A hankali ya zame ta daga jikin sa ya miƙe daga kan gadon , rigar baccin sa ya ɗauka ya saka , ya fara taku yana barin ɗakin , Yayi zurfi a cikin tunanin abun da ka iya je ya dawo cikin rayuwar sa , mama ita take ta kai kawo cikin ran sa , rayuwar ɗiyar sa yake hangowa , yana jin wani irin al'amari me girma wanda yake tafe da tsoro akan ta , yana son tsare ta , so yake ya boye ta kar laifin da ya aikata ya shafe ta , tsoro yake kar tarihi ya maimaita kan sa , Bakin cikin da yake shaƙa kaɗai a wannan daren yayi masa yawa ma , me yafi ka san cewa matar ka tayi tarayya da wani ta hanyar zina sanya bakin ciki da ruɗani a cikin rai ?? Wani irin kishi me tsanani yake ji , wani irin yanayi yake ji akan ta , ji yake ƙimar ta na zubewa tana zagwanyewa daga ran sa tamkar narkakkiyar roba a cikin wuta , ji yake tamkar yana ƙyamar ta , ," yaya maimounatu zata min haka,"??     Yake tambayar kan sa , yana sake maimaitawa ,   Meyasa ? Meyasa ? Wai meyasa ? Bai san cewa ya fito har harabar gidan ba sai da ya ji ƙaƙƙarfar iskar dake wajen tana ɗaga rigar sa da bai ɗaure maɗaurin ba , a hankali ya kai hannu ya ja igiyar yana ɗaurewa , Tun da ya fito idanun ta suka sauƙa a kan sa saboda daman ta gagara bacci ban da juyi babu abunda take , ita mace ce me zafin kishin abunda take so , dan haka sanin cewa da tayi yau ɗin biyamurdi zai kasance da gimbiya maimouna ya ta'azzara soyuwar ran ta , ya sa bacci gagara ɗaukar ta duk kuwa da iya satar sa ,    Dan haka ta fito ta barandar ɗakin ta dake sama tana iya hango gaba ɗayan harabar gidan ta kurkusa daga inda take , duk kuwa da sanin da tayi dare ya raba ƙarfe 1:30am , to amma zafin kishi haɗi da bagen so ai rufe idanun me su suke yi .   Me ya fito da shi a wannan daren ??    Ta tambayi kan ta Ta san shi farin sani kamar yadda duk wani motsi nasa yake kusa da zuciyar ta , take kuma iya fassara kowanne motsi nasa Kada dai inda ya saba fita ya tafi a dai-dai wannan lokacin ya nufa ?? Wani irin tashin hankali ta ji ya taso mata ,    Zato take ya daina ? Tunda tun bayan dawowar sa daga nigeria bata ji alamun fitar sa ba , bata kuma gan shi ya fita ba , Tunanin ta ya katse lokacin da ta ga ya ɗaga kan sa sama tare da waiwayowa sashin da take ,    Da sauri ta tsugunna tana ɓuya a bayan ginin gaban barandar , Cigaba yayi da kallon sashin nata lokacin da zuciyar sa ke kitsa masa wataƙila ita ma wannan ɗin da aka liƙa masa , ta riga ta gama sayar da nata mutuncin a waje , ya dangana kome da ya faru a matsayin hakkin baiwar Allah yakaka da ya ɗauka , ya jagorance ta suka aikata mummunan laifi , shi daman Alhaki ai kuikuyo ne .! ***** Asubar fari ya hau shiri , garin baki ɗaya yayi masa wari , so yake ya tafi , yana son zuwa ya ga mama yasan ganin fuskar ta ne kaɗai zai iya sassauta masa zafin da ran sa ke yi , Daga sashin sa kai tsaye cikin gida ya tasamma sashin hajiya umma ba tare da ya dubi sashin kowaccen su ba tsakanin sashin gimbiya maimouna da tun barin sa da yayi cikin dare da sashin siyama wacce bai ko kai da sanin launin kayan da suke cibge a ciki ba , Yana ratsa sararik gidan yana amsa gaisuwar bayu da hadiman da suke kai kawo suna gyaran gidan da sanyin safiyar . A falo na ciki ya tadda hajiya umma tana Azkar , gefen ta ɗan ƙaramin tire ne da aka jera gorar ruwa da ƴan kofunan gilashi , Tana ganin sa farin ciki ya bayyana kan sa bisa fuskar ta , cikar haiba da mutuntukar da ta hango tare da shi ya sa ya yi mata ƙwarjini a yau , tabbas aure cikamakin addini ne , cikin sa akwai martaba tare da girma me yawa , Gaishe ta yayi sai dai saɓanin da da yake shigewa kusa da jikin ta , yau ɗin tanƙwashe kafafun sa yayi a gaba kaɗan da ita ya sunkuyar da kan sa , Kallon tsanaki tayi masa ba sai ya faɗa mata ba ta san yana tare da damuwa me girma wanda a jiya kafin rabuwar su da yamma babu wannan damuwar a tare da shi , dan haka take hasashen ko menene damuwar sa tana da alaƙa da iyalan sa , ita kuma bata da burin zama ɗaya daga cikin iyayen da suke bincikar rayuwar gidan auren ƴaƴan su dan haka sai ta yi kamar bata ga damuwar ta sa ba , ta matsa zuciyar ta da ke son sanin meye ya same shi ? Yaya kwanan ɗiya na su dukkanin su da fatan kun tashi lafiya ? Basu da buƙatar wani abu ? Duk kowa lafiya umma na basu buƙatar kome ,   Umma zan tafi bakin aiki doumin an ƙira ni daga niamey bisa ga wani aiki na gouggawa da ya taso , Aiki ? Ba an baka houtu ba na tsawon sati gouda ? Umma aikin mu na kare rayuka da dukiyoyin al'umma ne koyaushe ana iya ƙiran mu kuma a kowanne yanayi da lokaci , ! Shiru tayi tana nazarin sa , kafin ta jefo masa tambayar da ta sanya shi ɗago kai Tare da siyama zaku tafi kou ? Shiru yayi kafin ya tattaro ƙarfin halin da ya yi masa saura      Niamey zan tafi ba dosso ba Umma , idan na dawo daga niamey zamu tafi dosso tare. bata jaa ba tayi masa addu'o'i kamar yadda ta saba tare da ƴan nasihohi , ƙarshe ta sake tunasar da shi girman nawin da ke kan sa a yanzu , ! **** Tunda ya hau kujerar zaman sa a jirgin da zai ɗaga da shi zuwa niamey ya zurfafa cikin tunani daki-daki , Da hantsi ya samu isa ƙofar gidan , kan layin shiru , da yake unguwar babu yawan mutane , ya cire ƙuɗin me taxi ya biya shi , ƙarasawa yayi jikin ƙofar gidan ya ƙwanƙwasa Hajja wacce take tsakiyar sharar ƴar harabar gidan ta saurara da kyau ta tabbatar cewa gidan nasu ake bugu , ta ajiye tsintsiyar ta ƙaraso jikin ƙofar ta tambaya wanene ?? Hajja ni ne ,     Ta shaida muryar sa dan haka ta zare sakatar ƙofar ya samu shigowa gidan , sai fara'a take masa tana lale marhabin da shi ,    Shiga ciki Babban soja bari na ƙarasa ture ɗan wajen nan zan zo mu gaisa , sannu ka sha doguwar tafiye ince kwana kayi a hanya ? Murmushi yayi ba tare da ya amsa mata ba ya sanya kai cikin gidan , Ƙiiii    Ƙarar turo ƙofar sa ta sanya ta ɗago kan ta ta dubi sashin da ta ji motsi ,    Hajja sannu da aiki ! Tace cikin ƴar muryar ta , Bai amsa ba saboda baki ɗaya hankalin sa da idanun sa na ga fuskar mama wacce take jingine da jikin falmata akan cinyar ta  , su duk biyun suna fuskantar , Taku ya fara yi yana jin yadda shauƙin son ta ke ɗibar shi , da sassarfa ya ƙarasa gaban su ya tsugunna gami da kai hannun sa ya kama ƴan kafafun ta da suke sanye da ƴar safa ya sunkuyo da fuskar sa ya sumbata yana me rufe idanun sa da jin yadda ƙaunar ta ke sake ratsa shi tare da wata nutsuwa ta musamman , me yake ƙauna irin ta tsakanin ɗa da iyaye ƙarfi tare da tsafta ??. Lokacin da ya ɗago kan sa falmata ta kawo hannunwan ta duk biyu ta ɗora akan fuskar sa , a hankali tayi yawo da hannuwan ta tana shafar fuskar sa da idanun sa ke rufe , Tamkar wuta ta jaa ta ta janye hannuwan ta da sauri , tana ɗauke mama ta ɗora kan kafaɗar ta ,   Da farko tayi zaton hajja ce ta shigo, sanin cewa daga ita sai hajja a gidan . Wa-waye ne ? Tace tana ƙoƙarin miƙewa ,       Koma ki zauna Fatima ni ne , Ya kai hannu yana ƙoƙarin karɓar mama , Ta gane muryar sa dan haka ta sakar masa mama a hankali , tana dai-daita numfashin ta da firgici ya sa shi hargitsewa , Yana karɓar ta yayi mazauni akan ɗaya daga cikin kujerun wajen ba tare da ya janye idanun sa daga kan ta ba ya shiga sumbatar kumatu zuwa goshin ta , Bai ko ji gaisuwar da falmata wacce ta zauna daga ƙasa a gefe take yi masa ba ,     ita ma shiru tayi ganin bai amsa ba Shigowar hajja ya sanya shi rungume mama a jikin sa suna gaisawa shi da hajja ,      Soja garin nan na ku kuwa ya karɓe ka , ka ga yadda kayi fes da kai kana ƙyallin fuska sai ka ce sabon ango ? Ah lalle miyar umma da zaƙi ta sa kayi shar da kai duk wannan hautsinewar sojin sun kau , ke Fatima kin kuwa gaishe da maigidan naki ?? Na gaishe shi hajja , To ban ga kin kawo masa ruwa ba , ? Zata miƙe ya dakatar da ita ƙyale ta hajja ita da take da larura baza ta iya aike ba ! Ƴar dariya hajja tayi Zata iya Babban soja ai matar ta ka ba dama akwai lura da kaifin ƙwaƙwalwa saurin gane waje ne da ita , ka ga dai ba mu rufa wata guda ba a gidan nan amma ta haddace kusan muhallin kome da kome da yake cikin gidan nan , ita da kan ta take zuwa ta ɗau ruwa a firiza ko ta je kitchen ta haɗa madarar mama , kullum addu'a nake mata Allah shi kawo mata waraka . Ɗan murmushi yayi yana duban falmata wacce ta koma ta zauna ta juyar da kan ta gefe , Kalaman hajja sun tuno masa da abunda ya so mantawa , watau kai falmata asibiti tare da samar mata gurbin karatu , Ya zama dole yayi duk wani abunda zai iya yi gurin kyautata rayuwar falmata ko domin ya samu girman laifin sa ya ragu a wajen Allah . Hajja ku shirya zamou tafi babban hospitalisé a duba lafiyar idanun fatima yanzu. !    To to yanzu kuwa , falmata tashi ki shirya bari nima na ɗan kintsa , ! Niamey national hospitalisé nan suka je , inda basu wani ɗau dogon lokaci ba suka ga ƙwararren  ophthalmologist , bayan haske-hasken da tarin tambayoyin da yayi mata akan idanun nata , a ɗakin gwaje-gwaje . Suka dawo ofishin sa inda youssouf ke jiran su , bayani ya soma yi masa daki-daki A sakamakon binciken da nayi a zahiri ban hango wata cuta ba a idanun nata sai dai raunin ƙwayar idanun nata watau ainahin jijiyoyin idanun suna da rauni , a tambayoyin da nayi mata nayi ƙoƙarin sanin tayaya ta fara samun rashin gani ko da shi aka haife ta ?  amma sai ta shaida min bata da masaniya akan mafarin samuwar rashin gsnin ta , A takaice cikin binciken da muka gudanar da kuma sakamakon amsoshin da ta bayar yayin yi mata gwaji da akwai yiyuwar dawowar wani kaso daga cikin ganin ta idan har za'a samu ƙwararrun kayayyakin aikin da zasu taimaka wajen dawo da ganin nata , Sai dai a halin yanzu bamu da waɗannan kayayyakin a nan gida niger da sauran ƙasashe masu tasowa , sai a manyan ƙasashen duniya da suka yi fice wajen samun ingantattun asibitoci masu isasssun kayayyakin aiki tare da ƙwararrun likitoci , Dan haka a yanzu abunda zamu iya yi mata kaɗai shine zamu bata magungunan da zasu iya taimakawa wajen bada kariya ga idanun nata daga kamuwa da wasu cututtukan da zasu iya kassara sauran ƙarfin jijiyar idanun da kuma hana idanun yin ciwo ƙaiƙayi da zubar ruwa ,    Da fatan kun fahimce ni ? Mun fahimta Doctor mun goude zamu dawou gare ka idan buƙatar neman taimakou game da asibitin da ya kamata a kai ta a wata ƙasar ya tasou mun goude ƙwarai Madallah . Washegarin ranar Biyamuradi bai zauna ba , ya shiga binciken makarantar makafi me kyau da yake son ya kai falmata ta fara karatu kafin lokacin da zai sake yunƙuri me ƙarfi akan lafiyar idanun nata a karo na biyu . Association Nationale Pour la promotion des aveuglés , nan ne inda ya ji gamsuwar sa akan ya kai falmata nan ta fara ɗaukar darasi , wacce jibiya ce ta koyar da makafi tare da basu tallafi me tushe daga ƙasar amurka , da ta tanadi ƙwararrun malaman makafi , Cikin sati guda yayi mata rajista da duk wasu abubuwan da ya kamata , ya samar mata da direba bayan ya sa an kawo masa ɗaya daga cikin motocin sa da suke maradi ya danƙa makullin ga hajja wacce take cike da farin cikin wannan cigaba da falmata zata samu a rayuwa . Ranar da zai bar garin zuwa bakin aikin sa jahar dosso , ya yi musu sayayyar kayan abinci da abubuwan da zasu iya buƙata tare da ƴar ƙaramar waya me sauƙin amfani ya ba wa hajja bayan ya zuba mata lambobin sa a wayar ya adana ta su a ta shi wayar , Suna zaune a falo yana musu sallama akan yau zai koma bakin aikin sa , sai kuma zuwan ƙarshen wani watan zai komo Godiya me tarin yawa hajja ta yi masa ,     Ya amsa tare da waiwayawa sashin falmata da take ta faman lila mama akan ɗan lilon ta wanda baban ta ya sayo mata su tarkacen kayan wasan yara iri-iri har da wanda ya fi ƙarfin shekarun ta , tun daga kan lilon yara , kekunan koyon zama har zuwa ƴar mota ta yara da ƙananun kayan wasanni irin na ƴaƴan gata na sosai  , bayan suturun da ya daɗa jibgo mata.    Fatima baki da wata matsala kou ? Shiru tayi tana ɗan lila mama a hankali ,   Falmata hala kin samu kurunta ? Kina jin Babban soja na magana kin yi shiru ? Uhum yau ni naga abunda ya shallake tunani na ,      Babu kome kawai ina son unmh     Uhum ina jin ki me kike so ?? A kaini makaranta   Ai na sanya ki makaranta fatima sati me kamawa zaki fara zouwa ,! Na islamiya ? Ina so a cigaba da koya min karatun addini ma ,! Toh babu damouwa idan Allah ya yarda zan bincika a samu me koyar da ke na Islama ma , Akwai wata damouwa bayan wannan ? Daman ka gaya musu zan dunga zuwa da mama makarantar ko ? Babu inda zaki dunga goyon ta kina tafiya da ita anan waje na zaki dunga barin ta idan ya so kafin ki dawo na sauya ta , ko kuwa na gudu da ita,  kina nufin baza ki maida hankali kan karatun naki bane ? Zaki dunga ɗaukar ta kina zuwa da ita makaranta ki ɓige da raino memakon karatu ni ke meyasa ana nuna miki hanya kina daɗa bauɗewa ne ?? Ɓata rai tayi ta ɗauke kai Murmushi youssouf yayi , shi dai rigimar hajja da falmata na ba shi dariya  Duba fatima ki bar mama a wajen hajja har ki tai école ki dawo Kin ji kou ?  Ba'a tafiya da yara école. Shiru tayi idanun ta na kawo ƙwalla ita dai bata ƙaunar abunda zai raba ta da mama ko na ƴan mintoci ne bare fa makaranta da awanni zata yi a can , kai anya zata iya , ? To hajja mu dunga zuwa tare da ke mana makarantar ? Sai ki dunga riƙe min mama nayi karatun na fito ? Ke raba ni da wannan gudun birin , gotai gotai da ni zani makarantar ? Yaushe rabon duniya da ayyaraye ?  Babu inda za ni ke kaɗai zaki tafi makarantar ki ki dawo ki same ni ina nan , ilmin ai shine Babban gatan ki falmata kin ji ko ? Naji hajja Yauwa mutuniyar ai shiyasa nake son ki akwai ki da saurin fahimta , Sallama suka yi da youssouf yana sake yiwa hajja godiya me tarin yawa tare da ɗanka mata ƴan kuɗaɗe wanda da kyar hajjan ta yadda ta karɓa sai da yayi ta roƙon ta da Allah  . Daga nan Dosso yayiwa tsinke bai jin marmarin zuwa maraɗi duk da cewa fiye da kaso talatin na ɓacin ran sa game da sha'anin sa da gimbiya maimouna ya kau , domin har sun yi waya ma cikin kwanaki biyun .    Assalamu Alaikum kowa da kowa ! Da fatan kuna lafiya ? Ina neman afuwar ku bisa jinkirin zuwan wannan shafin , hakan ya faru ne sakamakon tafiya da ni zuwa gida , ban samu zama ba ziyarar dangi da sauran Al'amuran yau da kullum . Da fatan zaku cigaba da haƙuri da tsaikon da ake samu cikin ajizanci irin na ɗan Adam ? Nagode     [9/3, 10:14 PM] +234 806 122 1116: Fikrah writers association MAFARI ( Hargitsin Rayuwa ) Umm'muaz 32 Bayan Shekaru Biyar Lokaci baya jira sai dai a jira shi , ba'a masa shamaƙi a yayin wucewar sa , Lokaci gudu ne da shi fiye da saurin  bugun zuciyar ɗan adam , Lokaci yayi juyi ya juya ya zo da sauyi ta mabanbantan fuskoki a rayuwar mutane a cikin tsawon shakaru biyar . Yakaka tana ɗaya daga cikin mutanen da suka samu sauyi ta fuska me kyau tare da tarin nasarori daki-daki cikin rayuwar ta , wanda a yau ta kawo matakin kammala makarantar ta secondry wacce ta rayu tsawon shekaru biyar tana faɗi tashin neman ilmi a cikin ta , da jajircewar ta tare da nuna ƙwazo ya sa aka ɗaga ta aka mata tsallaken aji na shekara guda daga jss3 zuwa ss2. Da hakan ya kawo kammaluwar karatun nata cikin shekaru biyar kachal . Ta fito da sakamako mafi kyau da ya sanyata farin ciki ita da duk wasu makusantan ta musamma malama maryam da lubna waɗanda da jajircewar su cikin taimakon yakaka a harkar ilmin ta har ta kawo wannan matsayin . Samy baby ma wacce ta tashi daga matsayin samy baby ta koma ,Hajiya samira ,"  ita ma ta taya yakaka farin cikin kammala karatun ta wanda duk wasu kuɗaɗen hidindimun karatun daga farkon sa har ƙarshen sa ya fito ne daga aljihun Alhaji Gali da har kawo yau suke liƙe a naniƙe da juna , bata da wata maraba da matar sa , kai har ma ta zarta matar sa ta aure iko da shi tare da samun kuɗaɗen hannun sa , Alhalin kuwa har yau da suke samun wajen shekaru takwas tare sun gaza yin aure ."illar bariki kenan ,! Karo na uku yakaka ta ajiye ƴar madaidaiciyar taɓaryar hannun ta da take dakan fura da ita , ta murza tafin hannun ta da suka yi ruwan hoda hoda saboda dakan da basu saba yin irin sa ba ,    Ta ɗago fuskar ta tana yamutsa ta , Ummi wallahi nagaji da dakan nan ɗan Allah ummi a min sassauci ki yadda na tafi ko'ina ne cikin garin nan na nemo furar nan nayi sadakar nan da ita , Allah bazan iya yin fura da hannu na ba , Malama maryam wacce take zaune daga gefe akan kujerar tsakar gida tana karatun littafin Al'mauduat Al'kubra , ta ɗan janye littafin daga fuskar ta    Fuskar ta babu alamun wasa ta ce ,    Sai fa kin daka furar nan yakaka kiyi sadaka da abunda kika sha wahala wajen samun sa yafi ɗaukaka darajar sadakar ki a wajen ubangiji , tsawon shekaru biyar kina faɗi tashin neman ilmin nan , a yanzu kin samu kin kai wata gaɓa me kauri ashe baza ki iya dakan fura kaɗai kiyi sadaka domin nuna godiya ga ubangijin ki ba ?? Jikin yakaka a sanyaye ta amsa    Zan iya ummi , To maza kiyi sauri ki gama dan shabiyu ta kusa , kar har  a sauƙo daga juma'ah baki gama ba kin ga kamata yayi a ce ki rabar da ita ga mabaratan da suke bakin masallacin juma'ar unguwar nan kin ji ko ?   To ummi tace tana saɓar taɓaryar ta fara daka ,    Lubna wacce take zaune a gefe kusa da ita kan ƴar darduma tana yankar ƙumba , ta ɗago kan ta fuskar ta da murmushi ta sanya hannu cikin faffaɗan kwanon silver da aka ajiye guntun dafaffiyar furar da ba'a kai ga daka ta ba , ta gutsuro wata ƙatuwa ta sake jefawa cikin turmin da yakaka ke daka ,    Yauwa ƴar ummi yi maza ki daka,  na ɗebo madara na fara damu ni ce ta farkon sanya Albarka a result ɗin nan kin sani ko ?    Ummi kina ganin ta fa ? Tana ƙara min wata bayan na kusa gama dakan   Lubna maza ajiye nails clipper nan ki karɓi dakan nan ki taya ta ,    Ta furta hakan tana gyara zama gilashin idanun tana cigaba da karatun ta .   Ummiii , dan Allah ni lokacin da nayi nawa dakan futar gama makarantar ta taya ni Haba ummi dan Allah,    Wallahi na taya ki kin manta ranar ....    Yanzu aikin samun ladan kuke yiwa haka ?    To shikenan duk ku bari ni zan zo na ƙarba nayi tunda da alamu ku lada yayi muku yawan da ya sa har kuka fara gudun sa ,   Da sauri lubna ta zaburo tana ƙoƙarin karɓe taɓaryar hannun yakaka ita kuma yakakar ta riƙe gam ta hana ta ,   Dan Allah ki bar ni na taya ki kin ji sahiba ta.     Tare da marairaice murya   Naƙi ɗin  , nima zan daka kaya na duk na mulmula na ɗau abuna a kai naje na rabar , kin ji sahiba ta . Wayar lubna da ta ɗau kiɗa ita ta raba musu gardama    Cikin sauri lubna ta ɗau wayar ta ta yi hanyar falo tana satar kallon ummi wacce bata nuna alamun ta san duk abunda suke a wajen ,   Yakaka ta bi bayan ta da kallo tana murmushi Ta kai gaf da shiga falon ta ɗaga murya tana cewa ,    A gaishe min da yayan namu da kyau da kyau kin ji sahiba ta ? Da gudu lubna ta ƙarasa shigewa falon tana dariyar jin kunyar ummi . Ƙarfe biyu dai-dai da idar da sallar juma'a yakaka da lubna sun kammala ɗaura fura guda uku uku a cikin farar leda tare da kindirmo me ɗan dama shima a ƙulle a leda daban , suka haɗa su suka zuba a ƴar bakar leda daban daban , ba laifi dayawa , Yakaka ta jaa hijabinta saka lokacin da ta gama saka socks ɗin ta a kafa ta zura hijabin tana kallon lubna wacce take ƙoƙarin ɗaura niƙaf ɗin ta ,    Sahiba dan Allah muyi sauri kar mabuƙata su watse ,     Taku biyu tayi ta ɗauko niƙab ɗin ta ruwan madara , mahaɗin hijabin ta ta  fara ƙoƙarin ɗaurawa a fuskar ta , Da sauri lubna ta riƙe niƙaf ɗin ,   Haba sahiba ta ? Ina mun yi cewa kin daina saka niƙab ɗin nan haka sai bayan kin yi aure ?? Hararar ta tayi    Shiyasa na ga ai kema yanzu da za ki fita babu naƙib ɗin a fuskar ki , ni dan Allah sakar min mahaɗin kwalliya ta , cikamakon martaba ta ,na sanya abuna ,    Amma ai ni kin san dai an riga an sanya rana , babu sauran wani ɗa namiji da zai sake cewa yana so na na kula shi ,    Ok to maza yi min gorin aure sahiba ,    Ta furta hakan muryar ta babu alamun wasa .   A hankali ta sakar mata niƙab ɗin , Allah ya baki haƙuri sahiba ba manufata ba kenan .  Mu tafi . Yakaka wacce bata furta zancen da wata manufa ta daban ba daga cikin ran ta sai domin ta samu lubna ta sakar mata niƙab ɗin ta da take neman ƙarfi da yaji ta hana ta sawa a cewar ta shi yake hana samari kula yakakar tunda ba ganin fuskar ta suke ba , duk sai ta ji ta ba daɗi da ta ga kamar zancen ta ya sa aminiyar ta a damuwa . Tafe suke akan hanyar su ta dawowa daga rabar da furar suna tafe suna hirar su hankali kwance irin ta shaƙiƙan ƙawayen da halin su da ra'ayoyin su suka zo ɗaya suke kuma ƙaunar juna domin Allah , Motar da take tahowa daga bayan su sannu a hankali saboda ruwan sama  da ya kwanta bisa kan kwaltar , wacce ta fito daga layin gidan su yakaka ,ita ce ta matsa musu hon , Su biyun suka haɗa ido , yakaka ta janye hannun lubna , da nufin ko Suna bisa hanya ne sun matsa daga hanyar , Maza biyu ne a cikin motar wanda kallo guda za'a musu a gane cewa ba ƙananun samari bane , mazaje ne waɗanda suke kan ganiyar shekarun su na 40 cif , wayewa tare da gogewar da ta bayyana kan ta a jikin su ita take nuni da tarin ilmin da yake jibge a ƙwanyar su , ɗaya yana mazaunin direba yayin da ɗayan yake daga gefen sa , Na gefen ya kai hannu a karo na biyu da nufin sake danna hon , na gefen nasa ya tare hannun nasa ,   Suleiman meye hakan kake kuma ? Yace yana kai kallon sa gare shi ,    Dan Allah abokina yi parking ka bani mintuna biyu zan fita ,   Bai ce masa ƙala ba saboda yanayin sa da bai tare da nishaɗi ya sa baya buƙatar doguwar magana , ya gangara daga gefe ya tsayar da motar , Da sauri suleiman ya fice daga motar , A hankali yayi musu sallama cikin nutsuwar da take halittar sa tun ƙuruciya , Tana jin muryar sa ta gane shi , shine dai maƙalemata manne matan da ya liƙe mata tsawon shekaru uku yana bibiyar ta ba tare da ta taɓa saurarar sa ba , Matsa hannun lubna da yake cikin nata tayi , ta mata alama da kar ta kula sa , sai dai irin nutsuwa tare da kamala da ƙwarjini na musamman da lubna ta hango a gare shi ya sa ta fahimci ba irin sa ne mazan da mata ke gwatsalewa ba dan haka taƙi amfani da umarnin yakaka ta ja ta tsaya tare da amsa sallamar sa  Baiwar Allah naji daɗi da ki ka tsaya kika amsa sallama ta domin nasan da ta ƙawar ki ce baza ku tsaya ba , dan kuwa tsawon shekaru kusan uku kenan ina bibiyar ta amma bata taɓa tsayawa ta saurare ni ba,   Da sauri lubna ta kai kallon ta ga yakaka wacce ta yi gaba kaɗan ta tsaya tare da ɗauke kai daga barin kallon su . Dan Allah kayi hakuri, tace da shi , girman sa na sake cika mata idanu Babu kome duba da cewa a yanzu bisa titi muke ba darajar mu bace yin magana anan dan haka ki sanar da ni adireshin da zan same ki ko kuma number ta wayar ki saboda ina son yin magana da ke game da ƙawar ki idan kin bani dama , Da sauri lubna ta ba shi number wayar ta , tana jin farin ciki na ratsa ta , a karon farko yau wani namiji ya nuna yana da ra'ayi akan yakaka , namijin ma gangariya irin wannan ai kuwa yau ummi na da farin labari . Bayan ya karɓi number yayi mata sallama ya juya wajen motar su , da ƴar dariya a fuskar sa ya dubi abokin sa da hankalin sa ke gefe guda da alama yayi zurfi cikin tunani . Abokina ka taya ni murna ga alamu na sanya ƙafa a kasancewa mijin mata biyu , ramla ta kusan samun abokiyar zama , tsawon shekara uku da nake bin yarinyar nan tana yin biris da ni , sai yau nayi sa'ar haɗuwa da ƙawar ta ga alamu ita zata min tsani na samun ta ,  na rasa me yake fusgata akan ta alhalin sau biyu kawai na taɓa ganin fuskar ta , Da alama akwai rabo ne a tsakanin mu me ƙarfi , A hankali ya tada motar ba tare da ya bada muhimmanci a zancen nasa ba , To ai sai ka ɗau harama , takaicin matan duniya ne bai ishe ka ba , ko kuwa ma nace har yau baka san wacece mace ba da irin tarin abubuwan ƙi da yake tare da ita da ace ka sani da baza ka yi sha'awar ajiye su har su biyu kamar kayan ado a gidan ka ba , Wuce su suka yi a hankali , Lokacin da suleiman ke bashi amsa Hamza kenan kai dai na rasa wanne irin tabo mace tayi maka a duniya kake musu irin wannan kuɗin goro , duk kuwa da yadda safiyya take tarairayar ka tare da lelen ka kamar wani jariri sabon haihuwa , bana jin ta taɓa saɓa maka a rayuwar zaman auren ku . Ya ƙarasa zancen tare da dariyar shaƙiyanci . Murmushin takaici doctor hamza yayi ,    Baza ka taɓa ganewa ba suleiman ! Ya maida ganin ga madubin  motar sa , yana hango ta ta jikin madubin ƙwarai tafiyar ta ta ɗau hankalin sa , mace ɗaya ya taɓa gani da salon takun nan , wacce bai ko son giftawar tunanin ta cikin ran sa sai fa yau da ya sake ganin wata wacce fuskar ta take a rufe  Bai kai ga ganin kamannin ta ba . Yakaka ashe daman irin zaman da kike da ni kenan ??   Cewar lubna idanun ta na bayyana ɓacin rai , A kaikaice yakaka ta dube ta , kin ga sahiba bana ciki da rigima , daga kawai mutum ...   Hmm   Lubna ta katse ta , Wallahi sahiba abu ɗaya zan faɗa miki a matsayin ki na wacce na ɗauka ƴar uwa , Kar ki yadda kiyi wasa da damar da ta zo miki , idan har wannan mutumin da gaske yake ki bashi dama ku fahimci juna , aka yi bincike bashi da wani aibu wallahi ki bada dama kuyi auren ku shekarun mu sun fara tafiya ishirin da biyu mun rufa ta da uku muke hari ,wallahi wasa ba namu bane dama kuma sau ɗaya take zuwa a rayuwa ,   Shiru yakaka tayi Kalmar ,"Dama," na maimaituwa a cikin kan ta , ita har tana da wata dama da ta rage mata kuwa ? Ai damar guda ɗaya da take da ita ta riga ta zo ta wuce tun a shekarun baya , " damar da mahaluki ɗaya ya bata wanda ta tabbatar baza ta taɓa samun  makamancin sa ba, bata yi amfani da damar ba a maimakon haka ma sai tayi masa mummunan sakamo da har yau idan ta tuno shi kunya tare da nadama basa ƙasa a guiwa wajen danne ta , ina ma ina ma ina ma ?? Da ace dama zata dawo mata ? Da ace zai sake ba ta dama ko da gutsire daga irin damar da ya bata a baya ? Wataƙila da ta gyara kuskuren ta ta wata fuskar , , abunda ta sani shi ɗin ya riga ya mata nisa ita ta zama wata shuɗaɗɗɗan lamari da ya taɓa giftawa cikin rayuwar sa , Bata da wani shauƙi ko tunani mai armashi akan wani ɗa namiji har yau ta gaza sake son wani ɗa namiji , " zata iya cewa ta ƙi maza ," ƙi irin na wanda kunama ta taɓa harbin sa babu shakka idan ya ga gizo-gizo kakkaɓe shi yake , dangantakar nesa nesa ce ke tsakanin ta da maza , shiyasa har yau ta gaza samun saurayi ɗaya tak , ita ce bata saurarar su bata bada fuska , take boye kan ta tare da killace surar ta daidai da fuskar ta a rufe take , ta zaɓi hakan , ta kuma fi son tayi tsarayuwar ta a haka ba tare da wani ɗa namiji ya sake ratsa rayuwar ta , burin ta ɗaya ne shine tayi ilmi kuma tana godiya ga Allah tana godewa malama maryam tare da addu'ar Allah saka da alkhairi ga baki ɗayan zuri'ar ta , Ko da ko kusa bata sahun malumma amma kai tsaye a yau ta wuce a ƙira ta da jahila , ta nemi ilmi tana kan nema kuma zata cigaba da nema har.....    Har suka kawo gida bata cewa lubna ƙala ba ,    Sai da suka shigo gidan ta ruga da ɗan gudun ta ta rungume malama maryam wacce take tsaye daga ƙofar kitchen tana amsa sallamar su .   Ni bazan yi aure ba har sai nayi ilmi na zama kamar ummi malama ta , sai ki san yadda zaki yi da mutumin da kika ba wa phone number . Murmushi ummi tayi ,    Anya kuwa yakaka ? Aure ai shine cikar darajar ɗiya mace Lubna wacce take zama akan kujera ta shiga bada labari tiryan tiryan tana yi tana hararar yakaka wacce take yanka musu cabbage da zasu ci abincin rana da shi . Sosai malama maryam ta yiwa yakaka faɗa daga ƙarshe ta ƙarƙare da yi mata nasiha tare da faɗa mata fa'idojin aure da girman matsayin sa a addini . Jikin yakaka yayi sanyi har idanun ta na tara ƙwalla , ta gaza cin abinci na kirki . A ƙarshe ta jaa kunnen ta akan daga yau kar ta ƙara ƙin saurarar duk wani namijin da yake da kamala da ya nuna yana son ta , ta ƙoƙarta ta saurare shi na ɗan wani lokaci ta fahimci wanene shi , daga nan idan ta yarda da halayen sa na ƙwarai ta bashi dama ita ma tayi aure , ko kusa kar ta kawo aƙidar ƙin aure kusa da ran ta saboda wani shuɗaɗɗan dalili nata , . A ladabce ta amsa mata da zata yi yadda ta faɗa mata . Bata wani jima ba saboda yadda walwalar ta tayi ƙaura ta musu sallama tana barin gidan ƙarƙashin rakiyar lubna wacce duk ta damu da rashin walwalar ƙawar ta ta , sai faman jan ta da hirar raha take , Har ƙofar gida ta rako ta , Zata tura ƙofar gidan ta shige lubna ta riƙo hannun ta , ta waiwayo tana kallon ta da sakakkiyar fuska . Sahiba idan baƙya son sa idan ya ƙira insha Allah zan faɗa masa dan Allah ki bar damuwa . Murmushi yakaka tayi ,    Ni dai ban ce miki ba , kawai ....shiru tayi ,     Baza ki gane ba sahiba . Zan gane dan Allah ki faɗa min meye ne ? Duk banji daɗi ba da naga ranki a jagule Ni bana son kowanne ɗa namiji ilmi me zurfi nake da burin yi saboda ina da mummunan rauni a zuciyata wanda jahilci ne ya assasa min ina so na samu ilmin da zai warkar min da ciwon da na ji akan jahilci , A hankali lubna ta gyaɗa kai tana sakin hannun ta ,   na fahimta, ta furta hakan ba domin ta fahimce ta da gasken ba , abunda ta daɗe da sani cewa yakaka tana da wani binannen ƙuduri wanda take dakon sa boye cikin ran ta da ita bata riga ta san wanne irin kuɗiri ne ba . Daga cikin niƙab ta sake yin murmushi ,    Sahiba sai gobe zan zo ki bani labarin yadda kuka yi da ,"direba,"    Ta ƙarasa zancen da dariya cikin muryar ta , ko kafin lubna ta bata amsa wacce ta yamutsa fuska tare da ƙanƙance ido   Ta shige gidan da ɗan gudun ta tana jin lokacin da lubna ke cewa daɗin abun ma direban jirgin sama ne . Da sallama ta shiga falon duk da cewa tayi ne ba domin tana sanya ran za'a amsa mata ba sai dan sanin muhimmancin sallama a musulunci da ta riga tayi . Kamar yadda ta zata kuwa daga samira har hamshaƙiyar ƙawar ta da take haƙimce akan kujerar falon babu wanda ya amsa sallamar ta , hirar su suke cigaba da yi da take cike da shewa da dararraki irin na yaran matan da suke juya duniya a tafin hannun su . Rage tsawo tayi ta ɗan durƙusa , Anty samy sannu da hutawa , Ke ke yaks wanne irin iskanci ne wannan ?? So nawa zan faɗa miki bana son kina shigo min gida da wannan maya-mayan yadikan da kike yawo da su a jiki , musamman ma na fuskar nan taki kamar wata korarriya daga makka ? To na faɗa miki yau ce rana ta ƙarshe . A hankali yakaka ta kai hannu ta kunce niƙab ɗin fuskar ta , lokacin da sofi take kai ganin ta kan ta , Kiyi hakuri anty na cire . To ya dai fi miki , yo Allah na tuba na sanya wannan mayanin a fuskata ai ya shaƙe min numfashi ya sheƙa da ni barzahu ban shirya ba , Kallon kallo suka yi a tsakanin su , kafin sofi ta janye idanun ta tana yatsina fuskar da ya zama halittar ta , Kirjin yakaka yayi dakan lugude , tsawon shekaru biyar bai isa a ce ta manta fuskar sofi ba matar da ganin farko haɗuwar su ta fari ta ɗau karan tsana ta aza musu ita da ƙanwar ta falmata , dan haka cikin hanzari ta miƙe tare da haɗiye kalaman gaisuwar da tayi niyyar miƙa mata , ta juya tana nufar ɗakin ta  . Friend wannan wacece ? Aina kika samo ƴar ƙwara ? Ko dai ko dai .... Ta ƙarasa zancen tana sakin wata shashashar dariya . Ɗan murmushi samy baby tayi cikin ran ta bata mamakin rashin gane yakaka da sofi ta yi , ko ita da kan ta bata gajiya da kallon yakaka , wata irin fata ce da ita wacce bayan haske tana ɗauke da wani irin taushi tare da ƙyalli a idanu , ya haɗu da gyara tare da jimaka me kyau da take samu daga ita samy baby , haɗi da girma tare da cikar macen da take kan ganiyar ƙuruciyar ta , sai ta zama tamkar farin wata idan ta gifta dole ta ɗau hankali , ɗan tsararren jikin ta da yake a murmure kowanne irin kaya ta sanya masa kyau yake . Ai ba domin tirjiya da yakakar take gwada mata ba da tuni maƙudan kuɗaɗe sun fara shigo mata ta hanyar yaks , amma wani ɗan lokaci kaɗan take jira wanda zata kammala aiwatar da nufin ta , ta kuma fara kwasar adashen da ta dunga zubawa a dalilin ta ,   Friend wannan wata haja ce da nayi tsintuwar ta a gari  ,     Kalaman samy baby suka zo daidai da zaman yakaka a bakin ɗan gadon ta , daga inda take tana iya jin muryoyin su ,    Daɗi ta ji da samy baby bata jaa dogon bayani ta sanar da sofi ko ita ɗin wacece ba . Taɓ kina nufin wanna ƙatotuwar budurwar kika bawa mafaka a gidan ki ? Ah lalle ,   ta ƙuta      Kawai dai dan ke ma ba miji ke gare ki ba , idan ba haka ba ina ke ina kawo annoba muhallin ki ?    Ai ni tsakanina da ire-iren waɗannan matan masu kama da barbarar yanyawa ko gaisuwar kan titi babu ,     Ai ko sama da ƙasa zasu haɗu bazan bar ido irin na yarinyar nan ya gauraya da na doctor na ba ,     Wai Allah har bugun numfashi na ya fara sassarfa bala'i .   Dariya samy baby ta kwashe da shi , daɗi na da ke freind akwai bala'in kishi ,     Sha kurumin ki sanya ranki a sassanyar inuwa tunda har kika mallaki doctor hamza a matsayin miji ke da kan ki kin san naki ne ke kaɗai mutuniyar ,     Wata sakaryar dariya sofi ta sake tare da ba wa samy hannun suka tafa . Ni yanzu kin ƙi ki faɗa min sirrin friend wai tsakani da Allah wacce duniyar kika samu haka a Boston da har kika ajiye waɗannan manyan kayan haka ? Kin gan ki kuwa sofi cikin shekaru huɗu jal kin sauya ta jiki , ai wallahi wanda duk  ya san ki a da da kike bulugari bazai gane ki ba a yanzu da kika koma wata katafila, ke ni anya kuwa doctor yana iya yin nisa da ke wannan irin abebaɗan more rayuwa da kika haɗa a jiki ahayye duniya gidan daɗi ɗan Allah ƙawata bani sirrin !    Kalaman samy baby na kusa da ƙarshe ya sa fara'ar fuskar sofi raguwa , Cikin jimami tace ,    Ai lamarin doctor ajiye shi gefe guda friend , kullum jiya iya yau ke wataran ma jiya ta fi yau ɗin domin ko yanzu kafin su kawo ni nan su ajiye baki ga yadda ya nemi min cin fuska a gaban abokin sa ba , akan sutura , wai kayan da na sa sun matse ni , bazan hau masa mota a haka ba sai dai na tafi na hau taxi shi babu abunda ya dame shi , ya dunga balbalin bala'i da daman ƙiris yake jira tun kafin mu baro US yake kumburi shi ɗaya uwa fulawar da yis yayi mata yawa,  ina dai lallaɓa sa ne , Wallahi tsawon shekaru uku da muka yi a US da zan lissafa miki irin baƙin cikin bawan Allah nan da na ƙunsa sai kin ji tausayi na , gangar jikin sa kaɗai na mallaka , ruhin sa na wani waje wanda nake zaton ya min nisa duk kuwa  ƙoƙarina akan kome nasa , ke dai kin san yadda daman aka yi auren nan namu , to duk da haka ban zauna ba malamai da bokayen yi nake na ƙarƙare miki ƙanƙat ɗin tsafi dai har india na je akan a min yadda zan yi na samu mazauni na dindin a gurin sa na amshi sararin zuciyar sa, Zuwa na karnataka india ne ma fa da aka min wani mugumugun aiki aka min filla filla da tunanin sa na samu yake kula ni har muke iya haɗa shimfiɗa , A hakan ban zauna ba kullum ni ce a gyara saƙo da lungu na jikina tare da matso kyau , rana ɗaya na lura kamar Yana son mace me manyan kaya , saboda bin wata mata da kallo da na ga yana ta yi a gidan cin abinci a boston , na dubi matar na ga idan banda himilin cinya da ɗuwawu bata fi ni kome ba , tun daga ranar na shiga faɗi ta shi ganin yadda zan yi nima na ajiye manyan kayan nan , magungunan ɗago ɗuwaiwai da ƙara faɗin cinya babu irin wanda ban afa ba , amma da yake jikin nan nawa marke ne , shiru maƙatau bulunbuƙui , jiya iya yau , na kasa haƙuri na faɗa miki tare da jagorar wata ƴar * ƙawa da nayi a boston balarabiya ce ƴar duniya ta ƙarshen ƙarshe  , ita ta kai ni aka min aiki me ƙanƙat , aka tatso tare da ɗago tudun bayan nan da kike gani , azaba babu irin wacce ban sha ba a lokacin aikin nan da bayan gama yin sa , amma na shanye , kuma babu shakka ƙwalliya ta biya kuɗin sabulu , domin wasu cin kashin da yake min da yawan fushin sun ragu , duk da dai da farko ya tada ɓallin sai na faɗa masa me naje nayi jikina ya koma haka ya dunga bincikata , da yake lokacin aikin nan na karnataka na kan zafin sa , zancen bai yi nisa ba ya manta ya kuma haɗu da shima yana son manyan kayan ai hajiyata shiru kike ji malam ya haɗiyi shirwa !    Sai dai ki ga idan na gifta yana zaune yana haka da ido ,"ta wani yi ƙasa-ƙasa da ido tana kwatance , " yana bin abebaɗan da kallo , ni kuwa sai na sake jujjuya masa su da kyau yadda zan sake kamo sa , a raina ina "faɗin kai da abubuwan ka ai daman sakin jiki kayi ka ƙure musu kallo meye na wahalar satan kallo kamar ba naka ba " ah to abun duniya menene ?? Sarkin fawa da kyautar ƙaho !     Wata ƙatuwar dariya me ɗauke da haniniya samy baby ta kwasa sofi tana taya , suka chafke   Shegiya tawan baki da kyau ! Watau shi tsuntsu me wayo ta wuya ake danƙar sa ,     Charaf kuwa     Ah to ai na faɗa miki friend babu abunda bazan yi ba babu kuma inda bazan shiga ba akan soyayyar doctor buri na ɗaya , shine ya kasance nawa ni ɗaya har abada ..    Kin kuwa kamo hanyar , ko ma nace kin isa ga matakin .!    Wata dariyar suka sake saki kamar sabbin mahauk.... Yakaka wacce dararrakin su ya mugun takurawa , saboda rabo da tayi da jin hayaniya sosai ya haka da kuma kalmomin su da basu mata daɗin saurare ta sanya ƴan yatsun ta biyu ta toshe kunnuwan ta , hakan bai mata ba sai ta ɗauko ƴar ƙaramar wayar ta wacce samy baby ce ta saya mata tana da memory a ciki wanda yake ɗauke da ƙira'o'in Alqur'ani izifi sittin tare da wa'azizzikan manyan malamai ta jawo ear plugs ta maƙala a kunnuwan ta , ta sanya ƙira'ar AlQur'ani ta fara saurara bayan ta jingina da jikin gadon nata . Niamey A ɗakin zaman marasa lafiya na musamman dake cikin national hospitalisé , mata biyu ne bisa kan ɗan gadon marasa lafiya , babbar ta jinginu da jikin sa ƙarfen gadon yayin da ƴar ƙaramar take kwance a jikin ta kan ta na bisa ƙirjin babbar dukkanin su biyu idanun su a rufe suke , Ɗan motsawa ƙaramar tayi tana yamutsa ƴar fuskar ta da take fayau ! Kafin ƴan daƙiƙai babbar ta buɗe nata idanun tare da tallafo ƙaramar ta miƙe zaune da ita sosai daga kishingiɗar da tayi ,     Sannu Mama , ya kike ji yanzu jiki ya daina ciwo ?     Duban fuskar maman ta tayi da raunanan idanun ta , ta kai ƴan hannuwan ta duk biyu ta ɗaura bisa fuskar mamar ta shafa tun daga goshin ta zuwa haɓar ta ,kafin cikin ƴar muryar ta me zaƙi irin ta yara masu wayo tace          Na ji sauƙi maama kin ji ko ? Da ɗan raunannan murmushi a fusksr falmata ita ma ta sanya hannu ta shafi fuskar mama yadda tayi mata ,    Naji daɗi mama na ta ji sauƙi ,Allah ya ƙara miki rangwame tare da sassauci , me zaki ci kafin ki sha magungunam ki ? ,    Mayar da kan ta tayi ta kwantar bisa ƙirjin mamar ta ,      Maama bana cin kome , ! Idanun falmata suka kawo ruwa tana jin wani irin ciwo daga ƙasan ran ta , ƙaƙƙarfan tausayin mama kamar kullum yana sake cin ran ta , da ace tana da dama da tayi musanyan jinin jikin ta da na mama wanda ke gauraye da ƙwayoyin ciwon da a kullum yake barazana ga rayuwar ta tare da sanya ta a tsananin ciwo , to sai dai bata da dama ciwon mama muƙaddari ne daga Allah tun lokacin samuwar halittar ta . Bai tare da cikakkiyar nutsuwa ya turo ƙofar bakin sa ɗauke da sallama , jin muryar sa ya sanya mama ɗagowa daga jikin falmata , ta waigo shi da buɗaɗɗun haƙoran ta ,   Papa !   Da sassarfa ya ƙaraso , ciɗak ya ɗaga ta tare da rungume ta tsama cikin jikin sa yana shafar lallausar sumar ƙan ta da take a tsefa an tufke mata ita a ƙeya . A hankali yayi baya yana zama kan kujera ɗakin ya tare da ajiye ta kan ƙafafun sa ya riƙo fuskar ta da hannayen sa biyu idanun sa na bayyana tsantsar damuwa da soyayya yace mata .    désolé ma chérie comment tu te sens maintenant ? ( sannu my dear ? Me kike ji yanzu?  Je me sens mieux maintenant papa!  ( naji sauƙi yanzu papa )     Ta furta hakan tana me shigar da kan ta zuwa ƙirjin sa ta kwantar da alamun rashin ƙarfi a tare da ita ,   Runtse idanun sa yayi da ƙarfi yana jin yanayin da ya gan ta a ciki na narkar da ruhin sa ,   A hankali ya ɗago kan sa yana duban sashin falmata daidai lokacin da ta kai ƴan yatsun ta tana ɗauke hawayen da ya biyo kan kumatun ta ,           Tausayin ta me ƙarfi ya taso masa ,      Fatimah , Ya ƙira sunan ta a ƙasan maƙoshi   Sashin da take jin tashin muryar sa ta waiga ba tare da ta amsa ba .   Meyyasa ba'a sanar da ni tashin ciwon mama ba ? Sai doctor ta ne daga nan ya ƙira ni yake sanar min ? Muryata ƙasa-ƙasa ta ce     Hajja ce ta hana a faɗa ma tace duk shekaranjiya ka tafi daga niamey , !      Miƙewa yayi tare da ƴar sa a kafaɗa bai ce kome ba , sai da ya kai bakin ƙofa yace mata     Bari mu tai ga likitan ta !      Bai jira amsar ta ba ya fice daga ɗakin .    Kichiɓus suka yi da hajja wacce take kan hanyar dawowa ɗakin bayan ta ɗan zaga ta motsa ƙafafun ta. Riƙe baki tayi nuna alamun mamaki ! O Ni , yanzu ashe Babban soja sai da ka taho ? Kai da shekaranjiya jiyan nan ka tafi bakin aiki ? Banda abunka ai mun riga mun saba mun kuma fahimci kan ciwon mama tana fara nuna alamun rashin lafiya da hanzari muke zowa da ita asibiti , ai da kayi zaman ka bakin aiki . Gaishe ta yayi a ladabce    ta amsa da sakakkiyar fuska .   Babu kome hajja ai lafiyar mama ta sa'a wuce aiki muhimmanci bari mu je ga likitan ta .    Bayan dogon bayanin da kamar maimaici ne gare shi akan cutar ƴar ta sa wacce take ɗauke da ciwon Amosanin jini , " da a turance ake ƙiran sa da Sickle Cell Anemia, Ya ɗora da yi masa bayani akan binciken da shi youssouf ya sanya likitan ya yi masa akan wannne asibiti ne mafi kyaun kayan aiki tare da ƙwararrun likitoci da zai iya kai ƴar sa ayi mata aikin da ake sanya ran idan har anyi sa da dacewa masu cuta irin na ta kan iya warkewa baki ɗaya . Fitaccen asibitin nan a duniya da yake ɗauke da ƙwararrun likitoci dake ƙasar amurka ,"Mayo Clinic ," shine asibitin da likitan ya tabbatar da ƙwarewar su akan aikin dashen ɓargo  ga marassa lafiyan da ya shafi manyan cutukan cikin jini . Miƙawa likitan hannu yayi suka yi musabaha lokacin da yake miƙewa akan ƙafafun sa domin barin ofishin . Likitan ya kai duban sa ga mama wacce tayi luf a jikin baban ta tana wasa da adon gaban rigar sa na soji . Madame Safiyya Baskore sommes-nous bien maintenant? pas plus d'injection non?    dariya  tayi kafin ta amsawa likitan dai-dai lokacin da suke ƙarasa barin ofishin ita da baban ta .    oui je me sens mieux maintenant plus d'injections . Dariya likitan yayi yana ɗaga mata hannu alamun ! bye bye !      A hankali ta motsa laɓɓan ta tana kwantar da kan ta kan kafaɗun baban ta   au revoir ! ( Bye ) ..       Assalamu Alaikum kowa da kowa !    Surprise ??  😂 Ina gaisuwa agare ku baki daya masu karatun da suke faranta min wajen Danna dan tauraron nan tare da ajiye min sharhin su a karkashin kowanne shafi na rubutu na,  ina son Sanar da ku cewa ina godiya me dinbin yawa agare ku. Okay ghost readers, Makaho bai San Ana ganin sa ba sai an zungura shi ko ?? 😠 Kun san bakwa kyauta min koh?     Amma ba kome a dai juri zuwa rafi wataran tulu zai fashe,  😂 [9/3, 10:14 PM] +234 806 122 1116: Fikrah writers association MAFARI ( Hargitsin Rayuwa ) Umm'muaz 33 Wannan shafin na bada tukuicin sa baki daya ga " ZULAIHAT RANO " MEELAH " RALIYA GARBA. #I MORE THAN APPRECIATE YOU SISTERS# Bayan an sallami mama daga asibiti sun dawo gida , idan banda lelen ta babu abunda falmata take rabon ta da makarantar ta ma yau kusan sati guda kenan , Domin duk yadda hajja ta so falmata ta tafi makarantar ta bar mata kulawar mama ta ƙiya , gani take daga ta matsa daga kusa da ita ciwon nata zai iya tashi . A zaune suke a falo hajja tana kishingiɗe tana hutawa bayan ta gama ƴan kananun aiyukan ta na safe , Mama tana kalmashe bisa cinyar falmata , wacce take bin duk gaɓoɓin maman tana tausa mata su sannu a hankali , jikin ta sanye da ruwan hodan kayan sanyi na yara mata me adon ƴan ƙula-ƙulai farare , ƙafafun ta a ƙunshe cikin fararen safar ƙafa . Biyamuradi ya shigo falon , a shirye yake tsaf cikin kakin sa na soji , fitowar sa kenan daga sashin sa da yake sabon gidan da ya saya musu wanda ya fi wanda suka fara zaman haya a cikin sa girma da tsari , domin wannan sashi uku ne da shi ƴan madaidaita , sashin da su falmata suke da sashin baƙi wanda ba'a amfani da shi sai kuma sashin biyamuradi da idan ya zo garin yake sauƙa a cikin sa a wasu lokuta , musamman a lokacin da ya tarar da rashin lafiyar mama , wasu lokutan kuwa a hotel yake zaman sa . Mama tana jin sallamar sa ta miƙe daga jikin falmata wacce take ƙoƙarin riƙe ta , Mama ki tafi a hankali kin ga ba wani ƙwarin jiki kika samu sosai ba , Bata kula ba Ta taka da ɗan gudun ta , da sassarfa shima ya ƙaraso ya chafe ta sama ya cillata , Yana juyi da ita kafin ya sauke ta zuwa ƙirjin sa yana dariya , Bonjour papa , ina kwana papa . tace daidai lokacin da take kai hannu tana ƙoƙarin cire hular kan sa , Taya ta cire hular yayi ya ɗora mata bisa kan ta da aka mata manyan kitson kalba suka zubo har kan kafaɗun ta , Bonjour mon cher ," yaya kin ka tashi ? Lafiya papa tace da shi daidai lokacin da take ƙoƙarin sauƙa daga ƙirjin sa , Ya sauƙe ta yana riƙe da hannun ta suka ƙarasa cikin falon , ya samu mazauni kan ɗaya daga cikin kujerun wajen yana gaisawa da hajja wacce ta miƙe zaune daga kishingiɗar da tayi , Kamar yadda ta saba , yanayin ta babu walwala idan har yana waje ta gaida shi , tana riƙo hannun mama wacce take ƙoƙarin ajiye mata hular baban ta a kai , Bata iya hana ta ba sai da ta ɗaura mata hular akan hular da take rufe akan ta wacce take mahaɗin doguwar rigar jikin ta ruwan madara me ɗan nawi saboda tashi da aka yi da ɗan sanyi garin sakamakon ruwan sama da aka kwana yi daren jiya . Shafa fuskar ta mama tayi , kamar yadda yake al'adar su ita da mamar ta . Maama kin yi chau dayawa , Papa ka ga maama na tayi chau , donne-nous des photos , ta ƙarasa zancen tana hayewa kan kujerar da falmata take ta zagaya ta bayan ta gami da sarƙafa hannuwan ta biyu ta wuyan falmatan ta cusa fuskar ta gefen wuyan ta ., Biyamuradi wanda ya fara yiwa hajja bayani game da shirye-shiryen da yake na tafiyar su US , ya juyo da duban sa kan su idanun sa suka sauƙa kan fuskar falmata wacce haƙoranta ke buɗe tana murmushin da yake bayyana farin cikin ta da ganin walwalar mama ya assasa mata , Kamar maganaɗisu ya riƙe shi , ya kasa janye idanun sa daga kan ƴar fuskar ta da komen ta yake ɗan madaidaici idan aka cire manyan idanun ta , Ba tare da ya iya ɗauke ido daga kallon ta ba ya zaro wayar sa daga aljihu , ya juyo baki ɗayan sa ya saita cemara ya haska musu hotuna wajen kala shidda , Da gudu mama ta sake sauƙowa ta dawo wajen baban ta , tana cewa zata ga hoto ? Ta ɗare cinyar sa , Batare da ya sake mata wayar ba ya nuna mata hotunan , da sauri ta sanya hannu tana sake tura huton gaba , fuskar wata ƴar baby me kyau kamar ta ya cika fuskar wayar , ƴar yarinya ce da bata wuce shekaru biyu ba tana tsaye a hoton , A hankali mama ta ɗago kan ta tana duban fuskar sa Papa bebe waye ? Zare wayar yayi daga hannun ta ba tare da ya bata amsa ba, daidai lokacin da hajja ta ke cewa , Wannan yarinyar da surutu kike kamar aku , duk kin bi kin tsare shi da surutu kin hana shi ya yi magana , bayan kuma yayi shirin tafiya aiki , ni zo nan ki zauna na miki tafiyar tsutsa a ƙafar ki . Sauƙa tayi daga jikin sa , maimakon ta tafi wajen hajja , sai ta nufi mamar ta , tana zuwa ta zauna a gefen ta gami da kwantar da kai a jikin ta tayi shiru , Boyayyar ajiyar zuciya Biyamuradi yayi , cikin ran sa yana hamdala da hajja ta katse masa tambayoyin mama , domin Alƙawari ya ɗaukarwa kan sa ba zai taɓa yiwa ƴaƴan sa ƙarya ba , akan duk wata tambaya da suka masa , sai dai ko ya sakaya amsar idan kaifin hankalin su bai kai su fahimce ta ba , amma a yanzu bai shirya amsa ba ga tambayar da mama tayi ma sa . Cigaba da yiwa hajja bayani yayi , inda yake sanar da ita , yana son ranar litinin ya zo su je ayiwa falmata da mama passport , zai fara nema musu visa Idan Allah ya yadda daga sun samu visa shi da su zasu tafi US , da ba zai wuce tsawon nan da wata ɗaya da ƴan kwanaki ba nan gaba , Ba shi da masaniya akan tsawon lokacin da zasu iya yi a chan ,saboda harka ce ta neman lafiya , bai san yadda lamura zasu kasance ba , amma dai visa ta tsawon watanni shidda zai samar musu . Ya ɗora da neman hajja ta masa bayanin duk wasu abubuwan da zata iya buƙata bayan kayan abinci da sauran abubuwan buƙata na rayuwar yau da kullum wanda zai iya kai ta watanni shidda ko fiye da haka , Da farko addu'o'in samun nasara akan abunda zasu nema tare da addu'ar nemawa mama samun waraka tayi ta jerowa , tana jin yadda tausayin su duk ukun ke kama ta , Babban soja , ni ba sai an min tanadin kome ba , saboda ka ga nima wajen shekaru biyu ake nema rabona da ƴan uwa da dangi , dan haka idan har tafiyar ta tashi , bayan kun tafi a washegari nima zan ɗau hanya zuwa nigeria nima naje na sada zuminci na ga ƴan uwa da dangi , shekaru sun fara jaa , mutuwar nan ta yanzu kar ta gifta tsakani ba'a nemi gafarar ƴan uwa ba , idan ya so bayan dawowar ku ko kuwa ma kafin ku dawo sai a sanar min nayi dawowa ta , ai ka ga nima na ribaci lokaci ko kuwa ? Babu shakka hakane hajja , to babu kome idan har tafiya ta kama lokaci yayi sai ki tafi zouwa gida kafin dawowar mu , Allah ya saka da Alheri , ki min duk wasu bayanai na abubuwan da kike buƙata da zaki yiwa mutanen gida tsaraba don Allah .! Toh madallah Babban soja , amma dayake nima a wajen nawa akwai ƴan kuɗaɗe irin waɗanda kake min kyautar su ai ba ma sai na maka lissafin kayan tsaraba ba , idan tafiya ta zo ni da kaina zani nayo ƴar tsaraba ta , A ah hajja , don Allah kar ki ce hakka , irin Alherin da kika mouna a rayuwa ba zamou iya biyan ki ba sai dai Allah shi saka da Alheri , ƙwarai ƙwarai ina miki godiya , ki min lissafi abun da kike buƙata duk zan sa a kawo kome ranar da zaki tafi sai direban da ya kai ki wancen karon ya sake kai ki nagode ! Ni ce da godiya Babban soja ni ce da godiya , Allah dai ya ƙara buɗi , ya ba wa mama lafiya , Ameen ameen hajja ya amsa yana miƙewa , Sashin da suke ya mayar da duban sa , mama har tayi bacci fuskar nan a chakuɗe alamun fushi take , Bai yi mamaki ba saboda sanin ta da yayi da saurin bacci , A hankali ya taka zuwa gaban falmata wacce tayi shiru , tana ɗan shafar kan mama da yake bisa cinyar ta , Fatima ni zan tafi bakin aiki zouwa le lundi zan dawo mu tai à muku passeport , ki kula da mama kar tayi wassa dayawa idan ta ji sauƙi sosai sai ta cigaba da zouwa école . Toh Allah ya kiyaye hanya ,! Ta amsa masa , Ɗan jim yayi a tsaye yana ƙure mata kallo da buɗaɗɗun idanun sa , hular ta shi ta karɓi yar zagayayyar fuskar ta me ɗan haske kaɗan , ji yake kamar ya bar mata hular a kan ta yayi ta kallon ta a haka , Jin yayi shiru kuma ta san da tsayuwar sa a wajen ya sa ta ɗan dago kan ta , tana sake haɗe fuska , Gyaran murya yayi ganin yadda tayi kicin-kicin kamar zata fashe masa da kuka . Fatima donne moi mon chapeau! ( miƙe min hula ta ) Ya furta hakan yana sake rage amon muryar sa , Falmata wacce tsayuwar sa akan ta da idanun sa da take ji suna mata yawo a jiki tamkar suna mintsinin ta ya sa ta diririce ta gaza fahimtar me yake cewa , ba wai dan bata jin yaren da yake yi ba , Mama bacci take . ta ce da shi tana fatan ya bar kan ta A hankali ya sunkuyo har tana iya jiyo hucin humfashin sa a fuskar ta  ya kai hannun sa guda ya zare hular sa dake kan ta , ya mayar kan sa . Na tafi Yace da ita yana juyawa ya bar wajen . Wani irin yanayi ta ji a jikin ta uwa wacce aka zubawa ruwan sanyi , har ga Allah ta mance da hular sa da take kafe a kan ta , Runtse idanun ta tayi da ƙarfi tana jin yadda zuciyar ta ke bugu . Hajja wacce duk abunda ya faru akan idanun ta tana iya hango su daga inda take . auho ! aikin banza ihu bayan hari , da kike wani runtse ido kina wani kawar da kai ya ƙadangariyar gobara , ai wallahi ni dai na daina saki a hanya kan sha'anin auren ki , tsakani na da ke ido ,! Ace wai tsawon shekaru fiye da biyar kin kasa zama cikakkiyar matar gida , ke kenan ɗaurewa miji fuska kina muzurai , zauna nan yarinya za'a yi bake lokacin da Babban soja ya gaji da halin ki ya sillo auren sa babu ni a masu yi miki dannar ƙirji , ko muƙamuƙi ba zan danna miki ba . Cikin rashin kulawa da zantukan hajja wanda falmata ta riga ta saba da jin makamantan su , tace Hajja ta me kika ce ? Abunda wancan yace , shi nace Ta amsa mata tana shirin miƙewa daga inda take tana cigaba da mita , Ƙatuwar mace kamar ki ace wai har yau tana da miji amma bata san amfanin sa ba sai rainon ƴa ,? Ai ni ina kamar ki nayi aure na na biyu ma , Ki ka ce me hajja ta ban ji da kyau ba ?? Na ce gidan ku ! Ta amsa mata tana ƙarasa barin wajen Murmushi falmata tayi domin ta san ta ƙular da hajja , Cikin ran ta tana juya maganganun hajja , Ban da abun hajja shi mutumin da kullum.take kumfar baki akan a kula da shi ɗin , shi ya taɓa nuna wata alama ne na kasancewar ta matar sa ? Tsawon shekarun auren su a tun bata san me takamaimai kalmar auratayya ke nufi ba , har ta zo ta san me ake nufi da aure ta hanyar malamar da take koyar da ita wacce a farkon fara ɗaukar darasi a wajen ta take yawan yi mata bayani akan auratayya a addinance da yadda mace zata kula da kan ta da mijin ta ta fuskar auratayya ba tare da kunyar kome ba cikin rashin sanin ta hajja ce ta yiwa malamar bayanin ƙarancin ilmi da wayon falmata ta kuma roƙi da ta dunga mata darasi na musamman akan auratayya , A hankali yau da gobe ta fahimci manene aure , matsayin miji a gun matar sa da matsayin mata a wajen mijin ta , Ta shiga ruɗani na sosai da har kawo yau bata fita daga cikin sa ba , " yaushe yakaka da Baban mama suka yi aure ?? Ita ba ta san lokacin ba kawai jin yakaka tayi da cikin mama . Akwai tsoro me tafe da son bada kariya tare da kyautata zato ga ƴar uwar ta yakaka , haɗi da son tsaftace mama shi yasa a duk lokacin da tunanin hanyar da aka bi aka samar da mama ya taso mata , take yaƙar tunanin da ƙarfi da yaji , bata son wani abu da zai aibata yakaka ya raɓi tunanin ta , Kewa tare da ƙaunar ƴar uwar ta bai ragu ba ko kaɗan a cikin ran ta sai ma zurfafa da yake sake yi yayi mata ƙaton miƙi a cikin rai . Rashin son suyi zaman auratayya irin na sauran ma'aurata da Biyamuradi ya nuna tsawon shekarun bai taɓa damun ta ba , Hasalima ta fi son hakan . Zaman mama take , tana rayuwa ne a ƙarƙashin sa kaɗai domin mama , za kuma ta cigaba da tsayawa ɗauke da auren sa a kan ta har abada muddin tana tare da mama . **** Daga niamey kai tsaye maraɗi ya wuce , bayan isar shi faɗa ya kai gaisuwa , kai tsaye ɓangaren sa ya nufa ba tare da ya shiga cikin gidan su wajen hajiya umma ba , yasan yanzu tana tare da jama'a masu neman taimako da ƴan barandar ta , sai zuwa yammaci zai shiga wajen ta zuwa lokacin ƙafa ta ragu a sashin nata .. Tattaki yayi zuwa sashin sa da yake bigire guda na gidan , bayun da suke kai kawo a fada su na ta kai gaisuwa bayan waɗanda ke take masa baya tun daga ƙofar fada . A bakin sashin sa suka jaa tunga saboda a tsarin sa bayi maza basa shiga ɓangaren gidan sa da matan sa ke ciki . Yana sanya ƙafar sa a cikin gidan ya ji wani yanayi marar daɗi na lullubar sa , hakan kuwa yana da nasaba da rashin daɗin zama a gidan da yake ji har kullum ya kuma rasa dalili . Taku ya fara yi da nufin isa sashin gimbiyar ta shi maimouna . Sai dai ƴan hannuwan da ya ji sun riƙe masa ƙafafun sa su suka sanya shi ya maida ganin sa ƙasa ,! Yumna Ya furta yana ƴar dariya tare da kai hannu ya ɗauki ƴar yarinyar da take ta yi masa dariya , ya ɗaga ta sama ya cilla ta tana ɓangala masa dariya . Rungume ta yayi a jikin sa lokacin da yake maida duban sa kan mamar ta wacce take ƙarasowa wajen fuskar ta ɗauke da murmushi , a shirye take tsaf , ba wata shahararriyar kwalliyar fuska tayi ba illa jikin ta da yake kiruf a rufe da babban mayafi tun daga wuyan ta da ya sha ado da tufafi irin na alfarma ,wanda ya amshi zubi da tsarin jikin ta na samɓaleliyar mace me zubin matan fulanin usul . Janye idanun ta tayi daga cikin nasa kamar koyaushe da bata iya jurar ganin cikin idanun sa duk kuwa da tsawon shekarun da suka shafe a matsayin ma'aurata , Barka da zouwa Baban Yumna , da fatan ka isso lafiya ? Lafiya mun same ku lafiya ? Yaya Yumna ? Ga ta tana lafiya , Ɗan shiru suka yi kafin ya katse shirun da tambayar ta Ina kuke da noufin zouwa da hantsi hakka ?? A ɗan ruɗe tace , zamu shiga fada gaishe da hajiya umma , Baza ku fita yanzou ba umma na tare da jama'a da wannan lokacin bani son idanun jama'a bisa ga kan ɗiya ta , ko dai ki bar ta ki tahi ke ɗai , ko kuwa ki bari da sanyin la'asar kun tahi tare . Ko kusa baza ta so ƴar ta ta gifta ta kurkusa da shigifar gimbiya moumuna ba bare har ta taka ƙafafun ta cikin wani al'amari da ya gifta a tsakanin su me girma , wanda ya tarwatsa takaitatcen zaman daɗin da suka fara gudanarwa a tsakanin su , daga nan aka yi walƙiya kowa ya shaida kowa , yayin da daga lokacin ta fara bin irin takun gimbiya moumuna da nazari , nan ta fahimci dayawa daga cikin boƴaƴƴun fuskokin ta masu cike da abubuwan al'ajabi tare da sarƙaƙiya da baki yayi kaɗan wajen furta su ga wani har sai idan wannnan mutumin ya ga kome a idanun sa . Hakan ya sa ta rufe kome ta haɗiye a cikin ta , ta kuma killace kan ta da ɗiyar ta daga gimbiya moumuna da ƴan barandar ta doumin ita ɗin ai gubba ce ga rayukan alhalin masarautar maraɗi ! Da sauri ta miƙa hannu tana ƙoƙarin amsar ƴar ta daga gare shi Mun hakure zouwa yammaci kamar yadda ka faɗi mouna Biyamuradi . Janye yumna yayi ya hana ta ɗaukar ta , a hankali ya kamo hannun tare da  sarƙafe ƴan yatsun sa a cikin nata hannun yana jin yadda taushin hannun ke tado masa da yanayin da yake ta dannewa tsawon satika , " muryar sa tafe da amo marar ƙarfi yace Mu tai ki ciyar da ni abounci na taho tare da yunwa me tsanani . Ƙoƙarin zare hannun ta take tana satar kallon sashin gimbiya maimouna , Cikin sa'a idanun ta ya sauƙa akan gnala shugabar bayin sashin gimbiya moumuna ta na abunda yake goge gilashin falon gimbiyar ta ciki a zahiri , wanda tashin farko siyama ta fassara abunda take da ɗaukar rahoto Toh Biyamuradi , amm... Shitt yace mata lokacin da yake jan hannun ta zouwa sashin sa kai tsaye da yumna saɓe kan kafaɗar sa ta dama tana ƙoƙarin ɗauke hular kan sa , Suka fara taku tare da masaniyar yau wajen ta ya kamata ya kwana a tsarin ƙwanakin girki . Gimbiya moumuna wacce tun isar sa fada ta samou labarin zuwan sa , inda bata yi ƙasa a guiwa ba ta tashi shirin tarɓar sa , Ta tashi hankulan bayun ta da aikin gyara gida wasu kuma na haɗa mata ruwan wanka tare da fidda mata kayan da zata sanya a jikin ta , Zuwa shigowar sa gidan ta fito daga wanka ta fara shiri , yana dosar gidan saƙo ya iso mata , hakan ya sa ta miƙe daga gaban mudubi ta ƙarasa gaban babban window na ɗakin ta dake sama ta raba labulen biyu daga inda take ta hangi kome da ya wakana tsakanin sa da siyama . Wani irin tuƙuƙi take ji yana taso mata daga cikin rai har tana jin ɗacin sa a maƙogoro . Meyasa ne wankin hula ya kai ta ɗare har tsakiyar sa ?? Lamarin da suka yi hasashen yiwuwar sa a watanni zuwa Shekara bayan zuwan ta masarautar maraɗi , sai ga shi shekaru har sun fara ƙoƙarin haurawa kirgen yatsu biyar ?? Wacce iriyar mummunar rashin sa'a ne gare su haka ?? Wanne sirri ne da yake boye cikin duhu da ya zamto shamaƙin da ya shiga tsakanin ta da cikar burin ta ?? Menene shi da ya wuce tasirin ƙarfin su ?? Tattare labulen tayi ta cukuikuye shi a tafin hannun ta tana jin kamar tayi girgiza ta fasa bango ta dira a sashin yarima youssouf ta kaddamar da manufar ta .. Ranki ya daɗe kƴakya..... Bata bari gnala ta ƙarasa kalmomin ta ba wacce ta shigo ta durƙusa daga bayan ta , Da hannu ta dakatar da ita , Ayi gaugawar shiryawa Biyamuradi abincin sa a aika da shi shiyar sa ., Ke zaki miƙa abincin da kan ki daga nan kin kawo mi ni labari na lamarin da ya auku gaba gare ki . Allah ya huci ran gimbiya ƴar sarkin nahiyar mu maigirma oumarnin ki shine abun bi .! da shigar su sashin nasa da yake me matuƙar girma , da tsari tare da wadatar tsaftar da ta haifar da kyakkyawan yanayi a wajen , Ya zauna bisa ɗaya daga cikin kujerun falon nasa , yana sauƙe yumna kan kafafun sa , siyama wacce ta saɓule mayafin ta ta ajiye a gefe ta sunkuya tare da yin gurfano a gaban sa , cikin nutsuwa ta kai hannuwan ta tana kunce masa igiyar takalmin sa tare da zare masa shi a hankali , Ɗan kiɗan da wayar sa ta yi dake nuna alamun shigowar saƙo ya sa shi zaro wayar daga aljihun sa ,    Lokacin da take ƙoƙarin karɓe hular sa dake hannun yumna ta ƙi bada hular ,     Ki bar mata hular mana , kin ka sani ko ɗiya tayi gadon baban ta ?    Da murmushi bisa fuskar ta ta wuce sama domin ajiye masa takalman sa , ta zo ta fara yi masa shirin girki .    Saƙon gimbiya maimouna ne mai ɗauke da tsararrun kalamai na barka da zuwa ƙarshe take sanar da shi ta bada saƙo a kawo masa ,   Fita yayi daga wajen adana saƙon yana shirin ajiye wayar hoton da ya ɗauke su ɗazu ya bayyana a fuskar wayar, Ƴan yatsun sa ya sa ya jawo hoton ya cika wayar ya na nutsar da idanun sa kan fuskar ta me ɗan haske kaɗan da  take ɗauke da wani sirri me tasirin da ya zarce a ƙira shi kyau , fatar ta suɓul-suɓul babu wasu ƙurarraji bare tabbuna manyan idanun ta da yankan su yake a tsaye da ƙwayar baƙi na cikin su me girma ne sosai , suna da ɗaukar hankali ta yadda ko yaya ta juya su sai mutum ya gan su ,   har kullum yana dogon tunani akan son sanin me ya makanta su ??   A hankali yayi ƙasa da hoton zuwa kan bakin ta da haƙoranta suke a buɗe tana dariya ,     Tsintar kan sa yayi da murmusawa, ya kai babban ɗan yatsan sa yana shafar fuskar wayar daidai zagayen ɗan bakin nata ,      lokacin da ya tuno da yadda take haɗe fuska ta tsuke bakin , duk idan ta ji motsin sa a waje , ta takura kan ta ta gaza walwala ,,   Kiyi haƙuri fatima ni ma ba zaɓi na bane irin rayuwar da muke gudanarwa a tsakanin mu a matsayin ki ta iyalina ,girman laifi na ya sa na gaza yin wani yunƙuri ,  ni ɗin me laifi ne a gare ki da duk ranar da gaskiya ta bayyana wataƙila baza ki yafe min ba , hakan ya sa na jinkirta miki har zouwa lokacin da kome zai bayyana agare ki , da na tabbatar ranar ta na zouwa , lokacin kike da zaɓi na zama da ni ko bari na bisa ra'ayin kan ki ,      Kiyi haƙuri Fatima zahra ina jin kunyar ki .       Ƙwanƙwasa ƙofar da aka yi ya sa shi kai duban sa ga ƙofar tare da mayar da wayar sa cikin aljihu    Daidai da ƙarasowar siyama wajen wacce kalaman sa na ƙarshe suka sauƙa cikin kunnuwan ta ,     Suka yi sanadiyyar harɗewar takun kafafun ta tare da sa zuciyar ta yin tsalle .   Wacece fatima ? Wanne matsayi ne gare ta da har Biyamuradi ke neman afouwar ta ? Shin laifin me ya aikata mata ?      Ruɗanin da ta afkawa ya hana ta tsinkayar kalaman da yake mata sai da ya ɗan ɗaga muryar sa da ƙarfi .   Siyama ki buɗe kofar nan saƙon maimounatu ne ya iso ,     Ba tare da ta amsa ba ta taka tana nufar ƙofar , cikin ran ta damuwa goma da ishirin ta san sarai saƙon ko na menene, abunda maimounatu ta saba yi mata ne a koyaushe , shine yau ma ta maimaita . Tana buɗe ƙofar tayi arba da gnala tare da wasu bayu biyu hannuwan su riƙe da manyan farantai da aka rufe su da tumaƙasa irin na alfarma ,    Ajiye faranta suka yi tare da yin gurfano a gaban ta ,   Ranki ya daɗe barka da fitowa !  saƙo ne daga gimbiya tace a shigar da kaɓaki ga maigirma yarima .    Fuskar ta a ɗaure ta ce Ki je sashi na yanzu yanzu ki ƙira min Rakiya ku zo tare ! Da sauri Gnala ta miƙe Ba ke ba .   Tace da kaushin murya   Ciki sauri ta koma ta tsugunna Ke tashi ki je ki taho da Rakiya    Tana nuni da ɗayar baiwar . Cikin ƙasa da mintuna uku sai ga su tare da wata yarinyar mace da zata iya zuwa sa'a ga siyamar ,    Ranki ya daɗe uwargijiya ta . Rakiya ki ɗauko waɗannan farantan ki biyo ni da su ,     Ta furta haka tana juyawa ciki Rakiya ta bita ɗauke da faranti guda , kafin ta dawo ta ɗau sauran da ɗai ɗaya ta shiga da su ,      Tana gama shigarwa ta fito gami da jan ƙofar , tana iya jiyo lokacin da uwargiyar ta ta murza ɗan mukulli , Kallon kallo suka yi tsakanin ta da gnala , kafin ta ratsa ta tsakanin su tana wucewa kan ta a ɗage bakin ta ɗauke da ɗan siririn murmushi ta fara rere waƙar da ta zo kan harshen ta a dai-dai lokacin   Aiki yayi kyau , tunda gida ya gyaru tsaf-tsaf ?    Allah kawo ran albashi mui fatantamawaaa . Na ku nawa ne ?  nawa kuka ɗauka a wata ɗaƴa ? In an bincika in an bibbiku da ɗai ɗai , har ma'aikatan zaria har ku na fi kowa ,  ɗan ɗan ɗaraɗanɗan .........   Da kallo suka bi ta tsaurin idanun Rakiya ba sabon abu bane a wajen su duk kuwa da cewa su sun fita daɗewa a gidan domin ita sabuwar ƴar aiki ce da ubbo ta kawo wa siyama tun daga jahar kanon nigeria .    Bata da kunya , bata kuma da tsoro ko kaɗan fallalliya ce ta ƙin ƙarawa . **** Fuskar ta babu walwala ta zuzzuba masa duk abincin da yake wajen akan wani ɗan faranti me ɗaukar ido , ta tanadar masa duk wasu abubuwan da ta san zai buƙata a wajen cin abincin ta mike tana barin wajen bata bi ta kan yumna ba wacce ta ɗau murfin wani ɗan kwano tana miƙa mata tare da yi mata gwarancin ta na yara , ta wuce ta tana nufar sama ,....    Ta ƙasan ido ya bita da kallo , ganin fushin ta a duk lokacin da maimounatu tayi masa aike ya haka ba sabon abu bane a wajen sa , siyama tana da zafin kishi shi da kan sa ya san haka , saɓanin maimounatu wacce tarin hikimar ta tare da wayo ya sa bata saurin bayyana kishin ta a fili har a fahimta ,   Shi da kan sa yana mamakin yadda ake maimouna take sanin zuwan sa maraɗi tun kafin ya iso gida ,Ko da kuwa bai sanar da kowa zuwan nasa ba , ya haka da yayi zuwan bazata , zai zo ya tarar tayo shirin tarɓar sa na musamman kamar daman ya sanar da ita zuwan sa ,  hakan ya sha faruwa ba sau ɗaya ba ba sau biyu ba maimouna tana iya sanin duk wani motsin sa a cikin maraɗi , wanda shi ya ɗau hakan a matsayin tsantsar kulawa , to ina laifin wanda ya kula da lamarin ka ??      Cigaba yayi da cin abincin sa cikin nutsuwa , yana jin yadda hoton fuskar falmata ke yawo a ran sa har ya hana shi jin daɗin cin abincin so yake ya sake kallon ta, dan haka ya sake ɗaukar wayar sa ya buɗo hoton , yana sake kallo lokaci lokaci yana cin abincin sa tare da sanyawa yumna a nata bakin . Abuja Yau garin an tashi da hadari bakikkirin kafin zuwa hantsi ruwa ya fara sauƙa kamar da bakin ƙwarya , Yakaka ita kaɗai ce a gidan ƙwal , saboda samira bata kwana a gidan ba tun jiya da yamma suka fita tare da Alhaji Gali . Gaba ɗaya bata jin ɗaɗin yanayin da ta ke ciki , gidan yayi shiru dayawa duk da dai ba shi da girma sosai , zaman shirun ya sa tunaninnika yi mata dirar mikiya , cikin kwanakin nan tunanin falmata da mama ya matsanta mata , ko dan karatun da ya ɗan tsagaita mata ne ? Amma koyaushe cikin tunanin su take ,    Yaya suke ? , ta san duk sun girma Falmata yanzu shekaru ishirin ne da ita babu ƴan watanni yayin da mama ta haura shekaru biyar , Tana begen ganin su duk da cewa samy baby tana tabbatar mata da lafiyar su , a cewar ta suns waya da Rahima wacce take sanar da ita halin da suke ciki , har ma ta ce yaya doctor ya sa su a makarantu , sai dai duk da haka tana son jin ko da muryar su ne amma anty samy ta hana a cewar ta ji daga garesu zai iys kawo tsaiko ga harkar karatun ta , zata yi rauni ta gaza maida hankali ga karatun ta , da jin hakan ya sa ta haƙurewa jin su , Ta bari har sai bayan kammaluwar karatun ta da samy baby ta mata alƙawarin zasu tafi maidugurin tare kamar yadda ta ɗauko ta ƙafa-da-ƙafa , ta je ta taya ta wanke kan ta a wajen falmata , yaya doctor , rahima da ma baba , ƙarshe kuma ta rungumi ƴar ta da ƙanwar ta su dawo tare nan .! Duk da cewa a farkon zaman su da samy baby ta kasa sakin jiki da ita ganin irin yAudarar da tayi mata ta rabo ta da maiduguri da ƴar uwar ta , sai ta kasance cikin ɗari-ɗari da ita tana tunanin ko zata yi yunƙurin cutar da ita sai dai abunda ya sa ta saki jiki bai wuce yadda lokaci yayi ta tafiya ba tare da ta ga wani sauyi na gallazawa , tilastawa ko ɓatanci daga samy baby ba ,sai ma hidima da take yi da ita tare da kyautata mata fiye da zaton ta , Tsawon shekaru biyar da suka yi tare samy baby ke ɗauke da nawin duk wasu buƙatun ta na yau da kullum , cin ta shan ta suturar ta kuɗin magani da na karatun ta duk ta dalilin samy baby ta same su kuma masu kyau masu inganci da suka taimaka mata ƙwarai ta fannin yin rayuwa me cike da inganci da isasshiyar lafiya tare da nasarar kammala karatun ta , Dan haka a sannu sannu samy baby ta mantar da ita girman laifi tare da yaudarar da tayi mata , a ƙarshe ta sake shirya mata sabuwar ƙaryar cewa suna waya da rahima , falmata da mama suna lafiya , wanda a zahiri ba gaskiya bane , hasalima rabon ta da shiga maiduguri ita ma ya doshi shekaru huɗu , kuma bata tare da number rahima , ba ta ma sake biyawa ta kan rayuwar bayin Allah biyun da ta raba su da garkuwar su ba , Ta tsara haka ne saboda yakaka ta sau jiki ta zauna tare da ita , yadda gaba zata cimma manufar ta hankali kwance ba tare da yakaka ta sake tayar mata da bori ba ! Sai dai kamar yadda suka alƙawarta lokaci ya zo da zasu maiduguri , idan ya so bayan dawowar su sai ta shiga jami'a kamar yadda samy baby ta sake ƙwaɗaita mata a cewar ta jami'a shine mataki na gaba da ya dace da yakaka , duk a ƙoƙarin ta na son janye ta zuwa kan turba irin ta ta , da take ganin fa a yanzu lokaci yayi . Ƙofar da ake bugu da ɗan ƙarfi ya sanya ta firgita ta dawo daga nisan tunanin da ta tafi . Duban agogo tayi ta ga ƙarfe goma sha biyu na rana ,   Fitowa tayi da nufin zuwa ta buɗe ƙofar da take hasashen dawowar samy baby .    Har lokacin ana yayyafi yif-yif da alamun yau yinin na marka-marka ne .      Da ɗan gudun ta ta ƙarasa bakin ƙofar ta zare sakatar ƙofar ba tare da ta waiwaya ba ta juya da gudun kar ruwan sama ya taɓa ta tana cewa    Sannu da zuwa anty samy .    Sai da ta tsallaka kan Balcony tukun ta juyo ,      A tsorace ta kai duban ta ga mutumin da yake tsaye a maimakon samy baby ,     Saurayi ne dogo wankan tarwaɗa yana tsaye ya zura hannun sa cikin wondon jikin sa , idanun sa sakaye cikin wani kwafcecen baƙin gilashi da kallo ɗaya za'a masa a fahimci rangwamen mutumcin dake tare da shi .    Juyawa tayi da sauri ta tura ƙofar falon ta shiga sabods tunowa da tayi da riga da wondon da suke jikin ta na bacci da duk da cewa basu kama ta ba ko kaɗan amma kaya ne masu tsantsi.    Kai tsaye ta shiga ɗakin ta ta fara bincikar hijabin ta ,    Sai dai hannun da ta ji ya sauƙa a ƙafaɗar ta ya sa hantar cikin ta kaɗawa ,   Da sauri ta jaa baya har tana gwaruwa da jikin wardrobe ,   Idanun ta ya shiga cikin na saurayin da ta bari a waje ,     Anty samira bata nan ta furta haka , muryar ta na karkawa , lokacin da take ƙoƙarin zira hijabin da ta samu nasarar ɗauka ,    Riƙe hajibin yayi da hannun sa ɗaya , yayi amfani da ɗayan hannun sa wajen zare gilashin idanun sa , mitsitsin jajayen idanun sa da suka sake shigewa ciki-ciki suka bayyana , yana bin ta da wani shu'umin kallo    Da muryar sa irin ta mashaya , yace   Wa yake ta samira tsahuwar guzuma ?    Ga kamar ki gorgeous , ya ƙarasa zancen yana kai hannu zai taɓa kumatun ta ,    Da ƙarfi ta make hannun sa gami da saurin zura hijabin ta ,    Ni ba ƴar iska ba ce kar ka sake taɓa ni , ka fita min daga ɗaki ,   Ɗan baya ya jaa yana yarfe hannun sa da ta buge bakin sa a ɗan buɗe alamun mamaki ,    Baby har da duka ?? Bata kula shi ba ta haura ta kan gadon ta ta dira tana nufar ƙofa , sai dai taku biyu kawai tayi ta ji ya kamo ta ta baya ya haɗa bayan ta da ƙirjin sa ya ɗaga ta ciɗak , ya shiga juyi da ita ,     To tunda wasan tsale tsalle kike so bari na miki hajijiyar ƙauna .     ya furta haka yana ɓaɓɓaka dariya . Tun ƙarfin ta ta fara ihu tana wutsil-wutsil da kafafu tare da ƙoƙarin son ɓanɓare hannun sa da ya zagaye cikin ta da shi , A guje samy baby da tun a tsakar gida ta fara jiyo ihun yakaka ta ƙaraso cikin ɗakin .     Kai kamal meye haka ?  kayi hauka ne ?? Dallah sauƙe ta .    Ba tare da ya sauƙe ta ba ya ce   Ke dallah kauce ki ɗan sakayo mana ƙofa zamu buga ƙwallo ne ni da wannan me zafin kan da tayi gigin duka na .   Ƙarasowa tayi ta jaa hannun sa ,    Kamal kar muyi haka da kai dan Allah ka sauƙe ta , ƙanwa ta ce fa , yaushe muka fara ƴar haka da kai mutumina ??   A hankali ya sassauta rikon da yayi mata kafin ya sake ta tana jin ya ajiye ta ta fita a guje , ƙafafun ta ko takalmi babu ,   Kallon baka kyauta ba samy baby ta wurga masa kafin ta ja ƙaramin tsaki , Kai dai kamal anyi tantiri ɗan iska , to bari na faɗa maka wannan haja ce me matuƙar tsada ba irin taku ba ce domin kuwa sabuwa ce fil , ba'a riga an shiga kasuwa da ita an daka mata wawa ba ,    Ba ta wasa bace na san a ɗan abunda ya shiga tsakanin ku a yanzu kaɗai ,laushin fatar ta da ka taɓa ya isa sanar da kai irin maɗuɗan da zasu taho ta hanyar ta muddin ta shiga kasuwa .      Ƙafar sa ɗaya dake sanye da wani ƙwamemen takalmi sau ciki ya ɗaga yana tokare ta da jikin gadon yakaka . Ni kuma kin san maƙudan da kike faɗa ba matsala ta bane , ko ruwan su kike so nayi miki kin san zan iya , muddin zan mayar ƙwaɗayi na akan wannan nunanniyar gwandar , nawa kike sa mata kuɗi ??   Two Million Naira    Ta furta cikin gatsali Bani account number da zan zira miki su ,      A ɗan jirkice ta dube shi cikin ran ta tana son ƙure shi , domin kuwa duk da sanin da tayi wa kamal na shahararran ɗan masu hali da iyayen sa suka gama gurɓata tarbiyyar sa , ya zama tamkar ɗan taure wajen bibiyar mata , manya da ƙanana kyakkyawa da mummuna shi baya zaɓe kawai dai idan ran shi ya biya ya samu ya maida mugun yawu shikenan kuma bai ƙara bi ta kan mace , bata zaton wasan sa da kuɗi ya kai ya haka .    A ɗage ta karanto masa account number da suna , cikin abunda bai gaza mintuna biyu ba sai ga wayar ta dake cikin jaka ta ɗau ƙara , Jikin ta na mazari ta fiddo wayar ta duba ,    Alert  ne na adadin kuɗin da ta buƙata cif .     Ɗan wara ido tayi da sigar mamaki , sai kuma ta kaɗa idon cikin yanayi na shanye mamakin ta irin na gogaggun matan bariki .     Babu shakka ka ɗau haja me girma , kuma na san baza ka yi wadarai da ita ba , yaushe kake buƙatar ta ?    Haɗe fuska yayi kafin ya watsa hannu    Ka duba wannan da wata maganar iska ? Irin waɗannan kuɗaɗen da na cire har sai kin min iyaka da ita ? Ai yadda ta sani haɗiyar mugun yawu dole daren yau na fanshe kuɗi na , daman ga gari ya ɗau sanyi yanayi ne na shiga daga ciki da sauri . Ta saki Wata dariyar da take bayyana farin cikin ta akan kuɗaɗen da ta samu da dama tana tsakiya da buƙatar su ,    Alhaji kamalu ,  to baka da damuwa ,  yanzu ka tafi , sai ka aika mun address ɗin da kake son na kai maka ita ni da hannun na zan miƙa maka ita anjima da dare ,   Kasan na faɗa maka sabuwa ce bata harkar nan to sai na maka yaƙin shawo maka kan ta , Ɗaga kafaɗa yayi cikin nuna halin ko oho ,      Ni dai ki tabbatar kin mata Wankan irin yadda ya kamata    Ya ƙarasa zancen yana kashe mata ido ,     Alhaji kamalu , kar ka ji kome .daren yau na kai ne a sama . Yakaka wacce take zaune dirshan a cikin ruwan sama ta jikin bangon ɗakin ta ta baya  ,   Ta kai hannuwan ta duk biyu ta toshe bakin ta a ƙoƙarin ta na hana kukan da take fitowa sarari kar su samy baby su ji , kamar yadda duk zantukan su ya ratsa kunnuwan ta .   Ashe daman anty samy yaudarar take akan kome , ashe burin ta ta tsundumata cikin irin rayuwar da tunda ta fahimci girman saɓon da ake aikatawa ta hanyar zina take yi mata addu'ar Allah ya sa ita ma ta tuba ta daina , Manufar ta ashe ta mayar da ita ga aikata zunubin da tayiwa ubangijinta Alƙawarin ta daina baza ta sake ba ! Ƙuka take da hawaye wani na korar wani , tana jin yadda tsoro ke mamaye ran ta , tsoron kowa da kome , tsoron sake yin zina ta hanyar tirsasawa , Takurewa tayi ta sanya fuskar ta tsakanin ƙafafun ta , sanyin ruwan da ya ɗan sake dawowa da ƙarfin yana ratsa ta ta hanyar jiƙa kayan jikin ta . Assalamu Alaykum . Gaisuwa tare da fatan Alkhairi a gare ku baki daya! Nagode.                            [9/3, 10:13 PM] +234 806 122 1116: Fikra writers association MAFARI ( Hargitsin Rayuwa ) umm'muaz 30 Babu kowa a harabar barikin sai masu gadi da suke daga kowacce kusurwa  , sakamakon dare da ya raba tsaka 2am , sai Biyamuradi youssouf da ke kai kawo a cikin hunturun sanyin da yake ratsa har ɓargon mutum gami da iska mai ƙura da take toshe ƙofofin hancin ɗan adam , a tsaye yake tsakiyar filin ya sunkui da kan sa jikin sa sanye da ƴar baƙar riga mai gajeren hannu da dogon wondon uniform ɗin su na soji , Ya zurfafa a tunanin makomar Auren da yake shirin karɓarwa kan sa nan da wasu ƴan awanni zuwa wayewar gari ,     Ina zai dosa da auren yarinyar ?? Yarinya ce ƙanƙanuwa , sannan kuma miskiniya , ta wacce hanya zai fara tallafar ta , domin ƙwarai take buƙatar matallafi cikin rayuwar ta da bata da kowa sai ƴar jaririyar sa ,     Me zai cewa iyayen sa su fahimce sa da dalilin sa na auren ta? Wanne irin hukunci maimartaba da hajiya umma zasu yanke masa idan suka ji ainahin abunda ya aikata da har ya kai shi ga auren yarinyar ?? Zasu su yi fushi mai tsanani da shi irin fushin da baya fatan ya gitta tsakanin sa da iyayen sa duk tsawon rayuwar sa ,     Me zai wakana tsakanin sa da gimbiya maimunatu lokacin da ta san ya auri wata mace kafin ita , Yana riƙe da auren wata bayan ita ? Zata iya yi masa kallon mayaudari kuma munafuki , a ƙarshe soyayyar su zata gurgunce da zai iya datse alaƙar su shi da ita , bai fatan haka saboda ya shaida irin tarin ƙaunar da zuciyar sa ke yiwa gimbiya maimounatu, Kalaman prof ya tuno inda yake ce da shi ,     Madallah tunda ka amince da auren Fatima , ka zo da wakilan/waliyan ka, a gobe zan baka auren ta , daga nan idan kana buƙata a goben zaka iya tafiya da ita tare da ƴar ka ,    A lokacin ya amsa masa da     Toh na Amince Har ya tashi zai tafi prof ya tsaida shi , To amma akwai wani lamari guda ɗaya , lamarin kuwa shine bazan iya ɗaukar yarinyar nan na baka ita , ka tafi da ita, ita kaɗai ba dole zan haɗa ka da mutum ɗaya wanda za ku tafi tare chan ƙasar ta ku domin a gano inda zaku zauna saboda sha'anin duniya , ta ka zo ta kan zo ko watarana wasu daga cikin dangin su zasu ɓullo su zo neman sanin inda ƴar su take , da fatan ka fahimceni da kyau kuma ka amince ?    Jim yayi a ƙarshe ya sake amsawa da    NA AMINCE Waje ya samu ya zauna akan ɗaya daga cikin dakalin da aka yi su domin zama dake a watse cikin barikin , Da farko yayi niyyar idan ya ɗauke ta ya kai su Niamey gidan ubbo a matsayin ƴar gudun hijirar da ya taimaka ita da baby mama idan ya so su kasance ƙarƙashin kulawar ubbo tare da shi har zuwa lokacin da zai samawa kan sa hanyar da zai bi ya bayyana su ga dangin sa ba tare da abubuwa sun rinchaɓe masa ba , Sai dai batun haɗa su tafiya da wani ya rusa wannan nufin nasa domin ko kusa ba zai so a san wasu dangi nasa ba , ba zai so asan ko shi wanene ba saboda kar watarana kome ya bayyana , a biyo sawu ba tare da sanin sa ba , kome ya lalace masa a lokacin , Idan kuwa har ya nuna ƙin amincewar sa , hakan zai sa a dasa ayar tambaya akan sa , ayi masa zaton marar gaskiya , wanda zai iya sa pro ya tsananta bincike akan sa wataƙila a ƙarshe kome ya isa ga masarautar su , bai fatan haka , Idan kuwa haka ne dolen sa ya yarda ya tafi da su da me rakiyar su , Ƙaunar ƴar sa da Allah ya jarrabe shi da shi ya sa duk yana ƙoƙarin fuskantar duk wani ƙalubale , burin sa ya tsira da ita , dan haka a ƙarshen tunanin sa ya ture duk wani ƙalubale gefe ya amince da mallakar baby mama tare da uwar goyon ta a lokaci guda da me rakiyar su , Yana tsaye a wajen aka yi ƙiran sallan farƙo na karfe 3:30am , kai tsaye ya nufi babban masallacin cikin barikin ya ɗaura alwala da sassanyan ruwan da iskar hunturu ta gama hura sa ya shiga masallaci ya fara jero nafilfili , yana roƙon Allah ya bashi nasara akan manufar sa ya kuma rufa masa asiri ya kawo masa warwaruwar al'amuran sa a sauƙaƙe , "toh ameen," ALƘAWARIN UBANGIJI ( MATAR MUTUM DAGA GARE SHI TAKE ) Da misalin ƙarfe goma na safiyar ranar Alhamis ɗin karshen sati ,  ƴan tsirarun mutanen da prof ya ƙira na cikin unguwa da basu wuce goma ba tare da wasu ƙarin mutane biyar da youssouf ya kawo a matsayin wakilan sa wanɗanda a zahiri abokan aikin sa ne daga ƙasar su , suka haɗu suka shaida ɗaurin auren FATIMA DILMARI , tare da YOUSSOUF ABDUL-AZIZOU BASKORE , wanda ya sauya suna zuwa youssouf Garba Malbaza Uzine, Bayan ɗaurin auren babu ɓata lokaci su abokan aikin youssouf suka yi komawar su domin ɗaura shirin tashin su zuwa Abuja inda zasu wuce ƙasar su ta jirgin sama a yau ɗin ,,  da shi kuma youssouf ya shigar da neman iznin a bada mota guda cikin motocin su na soji tare da direba da zai tuƙa su zuwa Niamey ta hanya , ba'a tsananta bincike ba aka bashi izni tare da shaida masa ya tabbatar ya samu isa niamey kafin ranar litinin inda za'a yi bikin dawowar su tare da yi musu ƙarin girma , Hajja me wurya," ita ce dattijuwar da prof ya zaɓa a matsayin wacce zata raka fatima ɗakin mijin ta daganan ta gano garin da zasu zauna a niger , kasancewar ita hajja mai wurya dattijuwa ce da a ƙalla ta tasamma shekaru hamsin , sannan kuma a halin yanzu bata da wani jigo cikin rayuwar ta iyaye duk sun mutu dangin kuwa kowa ta kai ta kai yake sannan tun asali bata da haula ɗan ta ɗaya ne tal da ta haife shi a shekarun girma bayan aure auren da tayi ta yi domin neman haihuwa , tana tsakiyar fara cin moriyar ɗan nata da ya ɗan fara tasawa shekarun sa ishirin da huɗu , ƴan tawayen boko haram suka shigo har gida suka yanka mata shi , a cewar su yana zagin su tare da sukar akidar su , dan haka suka kawar da shi, Tun daga nan rayuwa ta fara yi mata wahala , ƙunci da talauci suka dirar mata , zamani ne da kowa yake gudun wahala ba'a duban zuminci , tunda ta fahimci haka ta daina yin raragefe gidan ƴan uwa ta bazama neman na kan ta sanin da tayi da ɗan sauran karfin ta bata zama ƙarƙashin dangina ana zuba mata sharar walakancin , aikatau ta fara a gidajen saida abincin ,kasancewar ta gwanar girki iri iri ,musamman ma na ƙasar camaru da tayi farkon zaman auren ta a chan ,  amma sakamakon tsaurin ta da kuma tsayuwar ta kan gaskiya ya sa ba ta cika daɗewa a wajen aikin  ake sallamar ta , saboda bata zuru duk ta ga zalau sai ta tsinka ,"  daga baya ta koma aiki a gidajen masu hali nan ma gida biyu tana barin aiki saboda yadda take gwadawa uwargida iyakar ta a cikin gidan ta idan har ta ga abunda bai dace ba,  sai fa wannan karon da tayi dace ta samu aiki gidan Professor Mustspha dilmari  Allah ya tsawaita zaman ta a gidan da taimakon tarbiyyar yaran gidan da basu cika raini da walakanci irin na sauran ƴaƴan masu hali takwarorin su ba , babu kuma matar gidan shekaru biyu take nema da fara aiki a gidan a matsayin mai yin girki , musamman ma na shi prof . A jiya da prof ya ƙira su ita da falmata ya faɗa musu hukuncin da yake ƙoƙarin yankewa har ma ya tuntunɓi ita falmata akan jin ra'ayin ta , ta amince zata auri baban ƴar da take riƙo su tafi ita da shi da ƴar chan ƙasar sa ko kuwa ?? Ga mamakin sa ba tare da shayin kome ba Falmata ta amsa da ta amince zata auri baban baby ya tafi da ita tare da baby ,    Ƙwarai prof ya ji daɗin amsar Falmata domin da farko har yana fargabar ko yarinyar zata ƙi gatan da yake son yi mata na aurar da ita tunda ƙuruciyar ta , ga mutumin da yake iya hango nagartar sa a cikin yanayin sa da mu'amalar sa , yana hasashen mutum ne na ƙwarai ! A sarari ya nuna jin daɗin sa tare da yi mata addu'o'in samun nasara a rayuwa , sannan ya juya ga hajja mai wurya wacce ita ma take durƙushe daga gefen falmata , Hajja Alfarma zan nema a gurin ki akan ki raka fatima ɗakin mijin ta ki gano min wajen da zasu zauna ita da mijin ta a chan niger ɗin daga baya sai ki dawo. Da fatan zaki min alfarma ? Dariya hajja me wurya ta sa ! Babu kome Alhaji zamu tafi tare , me zaman aure ma ta amince bare ni ƴar rakiya ?? Ai ko gaba da binnin sin ne Alhaji ba na ƙi raka ƴar marainiyar Allahn nan ba , kai shima dai wannan dogon balaraben nijar ɗin Allah yayi masa Albarka da duk da kyan nan nasa da cikar zati irin ta ɗa namiji amma haka ya runtse ido ya ce ya amince zai auri wannan murɗaɗɗiyar bahaguwar yarinyar , ai dole ayi masa godiya bawan Allah . Nan dai Alhaji ya sallame su yana sake musu godiya akan biyayyar da suka ma sa , Kan hanyar su ta komawa hajja mai wurya tana riƙe da hannun falmata tace    Ke ƴar nan Allah ya dube ki ya tarfawa garin ki nono , irin wannan zankaɗeɗen miji da Allah ya wanke ya ba ki ?? Ai ko ɗiyar masu mulki ba ta ƙi shi ba , to zan fara faɗa miki tun wuri tun yanzu , ki zubar da waɗannan hargitsatsun halayen naki tun a nan nigeria kar ki ce zaki tafi gidan auren ki da su , saboda wannan dai miji naki wallahi kin yi sa'a wanke hannun ka taɓa Allah dai shi sa yadda surar nan tasa take halin sa yafi haka kyau , Ai bazan bar gidan nan naki ba sai na ga kamun ludayin zaman naki da shi , ato sai ki shirya ni ɗin dai da kika tsana kike ƙin bani riƙon jaririya , nice dai me miki zaman ɗaki sai dai muyi wacce za mu yi mahaukaci ya ɗau rigar kurma ... Zame hannun ta tayi daga cikin na hajja tayi gaba ta miƙa hanya , ƙalau tamkar me gani saboda yau da gobe ta fara haddace hanyar a ƙwaƙwalwar ta,    Sasakai hajja me wurya tayi    Au aikin banza kenan hanci ba ƙafa , to ki fi ruwa tafiya , nace ki fi ruwa tafiya , wannan yarinyar sai na dage kafin ta shiga hanya ta ɗau haske ta san me duniya take ciki kan ta hayaƙi yake ,! Falmata ko sauraron ta bata yi ba hasalima ji tayi hayaniyar hajja me wurya ta hana kwakwalwar ta sakewa tayi tunanin da ya kamata shi yasa ta zame hannun ta ta rabu da ita ,    Aure da ita da shi ?? Wanene shi da yace baban baby ne ? Da gaske shine baban baby ? Wanne irin aure zasu yi ? Ina ne ƙasar ta su ? Idan suka tafi zasu dawo ? Bata son barin nan inda take , burin ta watarana dr hamza ya nemo mata maman su , to amma yanzu kuma ga shi zata tafi ta bar nan ɗin ,     Abun da ta sani zata yi kome , zata tafi ko ina zata kuma ta shiga kowannen wahala domin ta tsira da baby mama , domin ta tsaya tare da baby mama , domin baby mama kar ta sha wuya , naƙasun ta miskinancin ta , rashin idanu , da ace ita lafiyar ta ƙalau , bata buƙatar abokin tayi wajen gina rayuwar ƴar ta , da zata gudu da baby mama ta ɓuya wani waje tana kula da ita , to amma ita ɗin ma miskiniya ce dole ne ta bi baban baby da yace zai kula da mama ƴar sa ce ! Ƙarfe biyu cif aka fara fito da jakar bocco ɗin falmata wacce ta haɗe kayan ta da na yakaka kakaf a cikin babbar baccon yakakar , sai kuma kayan baby mama shima a cikin babbar jaka , duk aka zuba su a bayan dunƙulalliyar motar soji me ƙirar golf kofa biyu , Biyamuradi youssouf ya taka zuwa cikin gidan falon prof , suka yi sallama inda prof ɗin ya bi shi da kalaman godiya ya kuma ɗora da damƙa masa amanar fatima tare da roƙon sa akan ya kula da ita , ita ɗin abar a tausayawa ce , Nan youssouf ɗin ya amsa tare da ɗaukar Alƙawarin zai kula da ita , Yana zaune hajja me wurya da falmata rike da mama haɗi da rahima suka shigo , falmata tana shirye tsaf cikin sabuwar atamfar ta ruwan ganye da adon furanni farare,  ta saka farin hijabi har guiwar ta , Daga gefe suka tsugunna , nan prof yayi musu addu'o'i tare da ƴan nasihu ya sake ɗanƙa amanar falmata a hannun hajja me wurya har lau , Daga ƙarshe ya zaro kuɗin sadakin falmata naira dubu ishirin sabbin bandir ɗin ƴan ɗari biyu ,    Ungo Rahima , miƙawa fatima kuɗin sadakin ta hakkin ta , fatima ina me baki haƙuri akan yadda auren ya zo a ƙurarren lokaci ban miki kome ba da iyaye ke yiwa ƴaƴan su idan zasu kai su gidan miji , amma na miki alƙawari na kuma yi magana da shi mijin naki akan idan kun isa ya tura min account number zan tura da kuɗin da za'a saya miki kayan ɗaki da na amfanin gida a chan kin ji ko ? Ki riƙe wannan sadakin auren ki ne , Da sauri falmata wacce idanun ta suka kawo ruwan hawaye akan irin ƙaunar da prof ke musu tare da sanin cewa yau zata bar gidan shi zuwa wani waje da bata da sani akan me zata je ta tarar , tace   Baba na bar maka kuɗin ni babu abunda zan yi da su ,   A ah fatima ki karɓa nace hakkin ki ne , watarana zaki samu abun saya da su ,   Muryar ta na karkarwar kukan da ta soma tace   Baba to ka riƙe min idan na dawo zan karɓa , Ba shiri hajja me wurya ta zungure ta , tana satar kallon youssouf da yayi shiru yana sauraran ta ,    Ƙasa-ƙasa tace   Ka ji min sakarya auren da tun baki kai gidan ba kike fatan ki dawo , ?? Kawo ƙuɗin na riƙe mata Rahima, irin kunyar nan ce ta amare take gwada mana ,    Rahima da take murmushi a hankali ta miƙawa hajja me wurya kuɗin , Madallah Allah ya sanyawa auren ku Albarka Allah ya sa abokiyar arziki ce , Allah ya kauda shaiɗanun aljanu da na mutane a tsakanin ku , Allah ya sa mutuwa ɗai ita zata raba ku, Allah kuma ya baku zuri'a masu albarka irin wacce manzo Allah zai yi alfahari da ita !     Laɓɓan Youssouf ne suka motsa a hankali da ,"Ameen .     Rahima ita ta raka su har bakin mota tana jin yadda kewar su take taso mata , ai anyi sabo zaman watanni tare , duk da cewa ta so tafiyar su tafi haka tsawo sai dai damar bata samu ba , amma ko babu kome tayiwa fatima murnar samun ɗanɗasheshen mijin da ya ƙere sa'an auren ta ta ko'ina hakkun fatima me sa'a ce .     Da wannan tunanin ta rufe musu ƙofar motar bangaren da falmata ta shiga inda suke zaune tare ita da hajja me wurya a bayan motar , Biyamuradi da direban sa suna gaba ," . ***** Tafiya ce suka ɗora ta miƙaƙƙiya tun daga maiduguri zuwa sokoto , inda basu samu isa sokoto ba sai cikin dare misalin sha biyu da rabi , alamun gajiya da suka bayyana baro-baro ga falmata tare da baby mama wacce ta ke yin ƙananun rikici na gajiya da rikon hannun ya sa youssouf ya kama musu ƴan ɗakuna a wani ƙaramin guess inn da yake cikin garin na sokoto zuwa wayewar gari sun huta sun kuma sake shiri sai kuma su faɗa yankin niger ta," ilela ," su ɗau hanya ta birnin N'konni da zai ɗaura su kan kodoben da za su sadu da birnin Niamey ɗin niger ....! Ba su suka samu isa Niamey ba sai ranar Asabat da misalin ƙarfe bakwai na dare duk kuwa da gudun da direban ya dunga shararawa tun da suka faɗa yankin niger kasancewar sun shigo ƙasar su , kowa yaga gilmawar motar su basu hanya ake , Kai tsaye direban ya wuce da su ( Radisson Blue hotel,) ƙarƙashin umarnin youssof , kasancewar shahararren hotel ɗin mafi yawan lokuta nan ne wajen sauƙar sa idan wani aiki ya kawo shi Niamey ɗin kasantuwar hotel ɗin kusa yake da manyan ma'aikatu masu muhimmanci na ƙasar da ke babban birnin Niamey , Babu ɓata lokaci ya kama musu ɗakuna inda hajja me wurya da falmata zasu zauna a ɗaki guda , (one bedroom Residence ) dake ƙasa shi kuma ya Kama nasa ɗakin a sama ( royal suite ) inda ya saba zama idan ya zo otel ɗin yayin da direba yayi tafiyar sa inda sauran abokanan aikin su suke ,  ya bar masa mukullin tare da motar , ' Bayan yayi wanka ya sallaci isha'i , misalin ƙarfe takwas da rabi ya sauko ƙasa , ɗakin da suke ya tasamma , ƙwanƙwas musu ƙofa yayi , Hajja me wurya tana sallar isha'i lokacin , falmata kuwa ta idar tana kwance bisa faffaɗan gadon ta sanya baby mama a gaba wacce take ta baccin gajiya bayan an cika mata ciki da madarar ta me ɗumi , Sake ƙwanƙwasa ƙofar yayi a karo na biyu yana sake kallon number ɗakin da take rubuce a jikin wani ɗan katako dake sakale a jikin ƙofar  ,"nan ne dai ɗakin nasu ," Miƙewa zaune tayi     Hajja kamar ana buga ƙofa ko ? Ƙyat ! Ƙyat    Hajja ta mata alama da hannu Oho sallah kike ? Sake bugun ƙofar aka yi da ɗan ƙarfi da ya sanyata miƙewa a hankali bayan ta zura hijabin ta , Ƙasantuwar ɗakin ba wani babba sosai bane taku kaɗan tayi ta isa jikin bango , dan haka ta fara shafawa bata sha wahala ba hannun ta ya sauka jikin ƙofar,     Waye ne ?    Ni ne buɗe min ƙofa     Ta shaida muryar sa   kama mariƙar ƙofar tayi ta murɗa sai dai bata ji alamun ƙofar ta buɗu ba , Ban iya ba   tace da shi cikin ƴar ƙaramar muryar ta ,    ,'Bata iya buɗe ƙofa ba ? Ya tambayi kan sa ,"   Hajiya batta cikin ɗakin ??   Tana sallah ,      ta ce masa   Bai ce kome ba ya gyara tsayuwa gami da jingina da jikin bangon ɗakin ,    Cigaba tayi da tsayuwa tana ɗan laluba jikin ƙofar ko zata ji wajen buɗewa ,    Ba'a ɗauki lokaci ba hajja ta idar da sallah ,     Ke kam wannan yarinya anyi bagidajiya , yanzu ace buɗe ƙofa ma kin kasa ? Ni gusa ki ban guri ,   buɗe masa ƙofar tayi ya shigo suka gaisa ,     Hajja akwai abunda kuke buƙata ne ?     Babu abunda muke buƙata ɗan nan , mun gode ƙwarai da hidima ,    Idon sa ya ɗora kan baby mama ,     Ta daina rigimou kou ? Ba ku buƙatar kome kou ? Shiru falmata tayi domin bata ma san da ita yake ba , Hajja ta ce fatima maigidan na magana       Wanne maigida hajja ?? Wata ƙatuwar harara hajja ta wurga mata , tamkar falmatan tana ganin ta  a ƙufule tace     Baban jaririyar ta ki A sanyaye ta ce me yace ? Wai zai tafi da baby ?   Da sauri youssouf yace Ban faɗi hakka ba fatima cewa nayi ba ku buƙatar kome ? Eh !    Ta bashi amsa tana zama bakin gado ta shiga laluben baby mama, hannun ta ya sauka bisa kan ta ta shiga shafawa a hankali , Ya juya ga hajja , ni zan shiga gari wajen aiki na , akwai yiwuwar gobe sai yammaci zan shigo , duk idan kun buƙaci wanni abu ku ƙira ma'aikatan otel ɗin ta kan wayar tarho ,   Ga ta nan ," ya nuna mata telphone ɗin dake ajiye daga saman ƴar durowar gefen gado  " madallah hajiya ina sake godiya Mune da godiya ai ɗan nan mune da godiya , to to babu kome Allah shi taimaka muna nan muna addu'a Ameen hajja sai gobe    Ya juya yana barin ɗakin Da sauri hajja ta zunguri falmata ,     Ke baki san ki gaishe da miji ko kiyiwa miji addu'a bane ? yau ni hauwa'u na ga abunda ya fi ƙarfi na me zan gani haka ? Yanzu ashe haka za ki dunga gwada rashin hankali a gidan auren na ki ? Ko kuwa taƙamar yarinta kike ? To bari ki ji na faɗa miki ni lokacin da aka min auren fari ma ban kai ki cika ba , kin fini ƙugu da ƙirji da sharaɓa da kome ke har shekaru ma domin ni lokacin da aka min aure ma sha huɗu nake ko nonon arziƙi bani da su , amma billahil azeem ban yi irin wannan haukar da na hango somi-somin ta a tare da ke ba ,     Ke kenan sai ƙwalafacin ƴa , alhalin kina gwadawa uban ta halin ko in kula , idan taƙamar ki son ƴaƴa ai sai ki kwantar da kai kema ki samu ki tara naki ba ki dunga gwada naci akan ƴar wasu ba ,    Falmata wacce ta fara jin haushin hajja akan takurar da ta ke mata,  muryar ta a cunkushe tace ,   To a ta ya zan tara nawa ƴaƴan ??     Sororo hajja tayi ,   Ah lalle abun naki na yi ne,  'an biyawa bazaura hajji , to sai ki cigaba da tambaya ta , ranar bada amsa tana zuwa , aikin banza yarinya sai sokonci kika iya ,.    Washegari biyamuradi youssouf bashi zaune bashh& har sai da ya samu wani ɗan madai-daicin gida irin wanda yake so a unguwar ,(Banifandou 2) ya kamawa su falmata hayar sa ya biya kuɗin shekara guda cif , Ƙarfe hudu tayi masa a shahararren company ƙera kayan katako da shirya gida ,(sunwe) inda ya faɗa musu buƙatar sa na son a kai masa kaya dai-dai da tsari da fasalin gidan sa , Basu yi ƙasa a guiwa ba suka tashi ma'aikatan su har su huɗu suka je ganin gidan , Hotunan gadaje , kujeru da sauran kayan adon gida aka dunga nuna masa tare da kuɗaɗen su , Bai yi zari ba ya zabi dai-dai kudin sa , tare da matsayin Falmata a wajen sa , Ma'aikatan da kan su suka kwashi kayan a motar su zuwa gidan inda gobe zasu je su shirya kayan da safe , Sai sha biyun dare Youssouf ya koma hotel ɗin saboda tun ƙarfe takwas na dare yana tare da manyan su suna wata ganawa ta musamman da lieutenant-Gènèral da Major Général , waɗanda sune ƙashin bayan samun ɗaukakar sa a fannin aiki , Ya so ya je ya ga ɗiyar sa da yadda suka wuni amma ganin yadda dare ya riga yayi  sai ya yi wucewar ɗakin sa kai tsaye , da zummar gobe zai gana da su cikin rashin sanin sa yini baby mama tayi da matsanancin zazzabi tare da mura , banda kuka babu abunda take , tun falmata na rarrashi ita kaɗai har hajja ma ta karɓa , duk da haka ta ƙi shiru , zuwa dare har shiɗewa take gaba ɗaya hankalin su ya gama tashi banda kuka babu abunda falmata take ko abinci sun gagara ci , Ganin duhu ya sawo kai ga youssouf bai zo ba ya sa hajja me wurya fitowa daga ɗakin ba tare da ta san takamaimai ina zata nufa ba , Allah ya taikaita mata wahala ya gama ta da ɗaya daga cikin ma'aikatan otel ɗin da ya kawo musu abincin rana , Nan ta tsaida shi ta tambaye shi ina ne ɗakin wanda ya kawo su ? Suna buƙatar taimakon sa , bai gane inda ta dosa a maganar ta ba saboda haka ya yi mata jagora zuwa gun manyan su , inda cikin kwatancen hajja me wurya tare da duba sunan ainahin wanda ya kama musu ɗakin da suke suka fahimci colonel youssouf take nema , basu da number wayar sa dan haka suka shiga ƙiran layin telfo na ɗakin sa nan ma basu ci nasara ba domin wayar tana ta ƙara ba'a ɗauka alamun da ke bayyana babu mutum a ɗakin . Ganin yadda hajja ta damu tare da sanin matsayin wanda ya kawo su ya sa suka tambaye ta matsalar su ? Nan ta shaida musu ƴar shi wanda ya kawo sun ne jaririya bata da lafiya suna neman a kai ta asibiti , Nan take ma'aikatan hotel ɗin suka jagorance su zuwa wani asibiti me zaman kan sa mafi kusa duba da halin da ƴar jaririyar take ciki na wahalar numfashi, bayan sun haɗa su da likitoci da nan take suka karɓi baby mama suka fara bata taimakon da ya dace , Sai suka dawo suka cigaba da ƙiran layin ɗakin youssouf lokaci-lokaci ko ya dawo ? Dan haka da shigar sa ɗakin bai rufa mintoci goma ba fitowar sa daga wanka kenan , kan wayar ɗakin ta fara ƙara , Nan ya ɗauka bayan sun gaisa suka sanar da shi halin da ƴar sa ke ciki tare da asibitin da suka kai ta , A gigice youssouf ya sanya kayan sa gami da ɗaukar ɗan mukullin motar sa , kai tsaye ya tasamma asibitin da ba baƙon sa bane domin fitatcen asibiti ne da duk ƙasar aka san sunan sa ,! Bai wani sha wahala ba illa tashin hankalin da yake ciki lokacin da ya samu ganin babban likitan da aka tabbatar masa shi ya kula da jaririyar a daren , A kiɗime youssouf ke tambayar sa ina ƴar ta sa take ? Kuma a wanne hali take ciki ? Nan likitan ya kwantar masa da hankali inda ya shiga yi masa bayanin abunda ke damun ƴar sa  tana da ,( single pneumonia )  wanda kuma shi ya kawo mata wannan wahalar numfashin tare da zazzaɓi me tsanani , sanadin shaƙar ƙura me ɗauke da ƙwayoyin cuta da tayi, Dan haka likitan yayi ƙira da a kiyaye sosai a kula da ita , a ƙarshe ya sanar da shi an shawo kan matsalar ta a halin yanzu har ma ta samu bacci zuwa gobe idan aka ga yanayin jikin ta ana iya sallamar ta , Tare da likitan suka nufi ɗakin da aka kwantar da baby mama ɗaki ne na musamman ( side room ) inda falmata da hajja suke tare da ita , Lokacin ƙarfe ɗaya saura na dare dan haka nuna masa ɗakin ya yi , ya juya , A hankali ya murɗa kofar ɗakin ya shiga , da haske wal a ɗakin dan haka ya hango falmata daga kan gadon tana zaune ta jingina bayan ta da jikin ƙarfen gadon tana riƙe da baby mama a hannun ta , ga alama bacci take , Hajja kuwa tana kwance akan ƴar shimfiɗar da ma'aikatan asibitin suka bata sai sharar bacci take saboda gajiya da tayi da kuma jikin girma ! A hankali ya tako cikin ɗakin ya ƙarasa bakin gaɗon gami da rage tsawo ya leƙa fuskar baby mama , ya yi haka ne saboda baya son tashin su a bacci, Falmata kuwa tun taɓa ƙofar da yayi ta ji sa , hasalima ba nisa baccin na ta yayi ba saboda sam yanayin wajen da yayi shiru sosai yana bata tsoro , tun tana ƙiran sunan hajja lokaci zuwa lokaci tana amsa mata har dai ta ji hajjan tana mitar ta dame ta da ƙira cikin magagin bacci dan haka ta haƙura ta ƙyale ta , Tayi shiru tana sauraran sauƙar numfashin baby mama da take yin sa cikin nutsuwa alamun sauƙi ya samu gare ta , Hannun sa ya kai a hankali da nufin ƙara rufe jikin baby mama da ya ɗan buɗu kaɗan ba tare da sanin falmata ba , Yana ajiye hannun sa ta maida nata akan nasa ,    Ɗago kan sa yayi ya dubi fuskar ta , manyan idanun ta da suka ɗan yi jaa kaɗan sun kafe fuskar sa da kallo tamkar tana ganin sa ,    Haɗa baki suka yi wajen yin magana ƙasa-ƙasa    Ita tana tambayar wanene ?   Shi kuma yana cewa ni ne fatima ! A hankali ta ɗauke hannun ta daga kan nasa ,   Shi kuma ya gyarawa baby rufuwa tamkar yadda yayi niya cikin ran sa yana mamaki tare da girmama nisan kunnen ta tare da yadda take kaffa-kaffa da ƴar baby , da ɗai bai taɓa cin karo da uwa irin ta ba , duk da ƙarancin shekarun ta Komawa yayi ya zauna akan ɗaya daga cikin kujerun wajen yana duban fuskar ta cikin nazari , kallon ƙurr yake mata tsaf yana wasu tunaninnika masu nissa , A jikin ta take jin idanun sa suna yawo saboda tsikar jikin ta da ta ji tana mimmiƙewa,! ya tsinkayi muryar ta da ɗan karfi tace .    Ka ɗaina kallo na haka bana so ! Ware idanu yayi da ɗan mamaki a fuskar sa ,"ya aka yi tasan ina kallon ta ,"? kafin yayi murmushi kaɗan ganin yadda ta turɓune fuska , ,'Ƴar baiwa ce," ya aiyana haka cikin ran  sa , a sarari kuwa cewa yayi     Ki kwantar da itta ke ma ki kwanta dare yayi ,!       Yayi baya da kan sa tare da miƙe dogayen kafafun sa ya ɗan zame kaɗan akan kujerar yana jin yadda tunanin lamura suke yi masa rubdugu tamkar yadda ya saba duk dare tunda abubuwa suka fara haɗe masa ! ***** Stade Général Seyni kountchê ( SGSK ) nan ne babban filin da gwamnati ta shirya gudanar da bikin karamma sojojin ta waɗanda ta tura nigeria tare da yi musu ƙarin girma , har ma da kyautuka ga waɗanda suka chanchanta , ! Mai martaba sarkin Maradi tare da Mommoudou , 'wanda hajiya mama ta tilasta masa zuwa taron ƙarin girman ," sai Tafeeda ƙarƙashin rakiyar tawagar maimartaba , suna cikin mutanen da suka halarci wannan taron da suka samu isowa a yau , sai kuma Ubbo tare da Siyama wacce ita ma ta iso Niamey tun ranar asabat tayi zango a gidan ubbo tare da cigaba da tsara yadda zata fara bin matakin farko na kusanta kan ta ga Biyamuradi muradin zuciyar ta ! Da wasanni irin na soji , kiɗe-kiɗen su zuwa faretin su , aka fara buɗe taron da kai tsaye ake watsa shi a gidajen tv dake baki ɗayan ƙasar Niger , Kafin a bada dama ga maigirma Shugaban ƙasa yayi jawabin yabo da jinjinawa ga sojojin ƙasar sa , sannan shugaban rundunar sojojin ƙasa na ƙasar ma yayi nasa bayanin , har zuwa kan wasu manyan kusoshin gwamnatin ƙasar da manyan soji da duk dai yabo ne suke yi ga sojojin su da suka dawo daga bakin daga , Youssof Abdul-azizou shine wanda aka fara ƙira domin martaba shi tare da yi masa ƙarin girma , Da faretin su na soji ya fito filin ya ƙarasa har zuwa gaban shugaban ƙasa ya sara masa ya juya gaban manya-manyan sojojin su na ƙasa nan ma ya sara musu kafin ya ƙarasa kan ɗan tudun da aka tanada domin tsayuwar sa inda shugaban sojin su na ƙasa yake tsaye , daga gefen sa wasu sojoji biyu ne a ƙame da ƙwali rike a hannuwan su  , Sara masa yayi ya ƙame , cikin takun sa na soja lieutenant General ya ƙaraso gaban youssouf tare da kai hannun sa ya warware ɗan yadin dake ɗauke da tambarin girman matsayin youssouf ɗin a soja , ya miƙa sa ga ɗayan sojan dake hannun sa na hagu ya sa a kwalin hannun sa , lokaci guda ya waiga ga ɗayan sojan ya ɗauki sabon rank ɗin da ke ɗauke da zanen yellow layi huɗu wanda yake ninke cikin kwalin hannun sojan ya maƙala a gefen kafaɗar youssouf ɗin dai-dai inda ya cire na farkon , Da hakan yake nuni da sabon matsayin Youssouf Abdul-azizou Baskore da ya tashi daga colonèl ya koma MAJÓR YOUSSOUF ABDUL-AZIZOU BASKORE , A take gurin ya ɗauki tafi tare da sarewa da gangunan su na soji , wani irin yanayi ne ya bayyana a fuskar mommodou da take kirtiɓ ya haɗe girar sama da ta ƙasa , idanun tafeeda da ya sauƙa cikin nasa shi ya sa shi gyara yanayin fuskar sa tare da haɗa hannunwan sa biyu cikin yanayi na dole ya ɗan tafa su ,! Da fareti major youssouf ya dunga bin su ɗaya bayan ɗaya tun daga kan shugaban ƙasa har zuwa shuwagabannin sa wajen aiki yana sake sara musu , masu camera na aikin haska shi da masu ɗaukar sa a  video ,  ƙarshe ya dire a gaban mahaifin sa da yake hakimce cikin shigar su ta sarakuna , idanun sa da suke sakaye cikin farin gilashin ƙarin ƙarfin ido suna bayyana tsantsar farin cikin da yake ciki , yayin da bakin sa da yake rufe ta cikin rawanin sa yaƙi daina murmushi , Ƙamewa yayi ya sarawa mahaifin sa , ga jin daɗin sa sai maimartaba ya miƙe gami da miƙa masa hannu suka yi musabaha idanun su na musayar zallar ƙauna , ya rungumo shi zuwa jikin sa ,    Bakin sa na furta kalmar   MADALLAH DA KAI MAJOR YOUSSOUF KAI KA KASANCE ABUN ALFAHARI NA ,    Kunnuwan youssouf kaɗai suka jiyo me mahaifin nasa ke cewa . Yayin da fuskar mommodou tayi jaa tana tsattsafo da gumi . Ware idanu sosai hajja me wurya take cikin son tabbatar da fuskar wanda take gani tarwai a fuskar ƴar tv da take kunne cikin ɗakin su na hotel da basu fi mintoci ishirin da dawowa cikin sa ba daga asibiti da aka sallamo baby mama wacce tayi sumul da ita tana ƴan wasanni ta tamkar ba ita ce jiya ta sha wahala ba ,    Ke fatima wannan ba mijin naki bane ake masa ƙarin girma a wajen aikin sa? Ga shi nan ana nuna sa a tv,?  ashe babban SOJA kike aure , ah ki ce shiyasa kike firirita , ashe matar soja ce ,    SOJA ? waye ne sojan ? Ita fa bata ƙaunar soja ko jin sunan su ta yi zuciyar ta tsinkewa take , mutanen da suke da bindigogi da jiragen yaƙi ita kuwa ai bata manta bama-baman da sojoji suka dunga sakar musu a daji ba, da har ya sa ta gurɗe ƙafar ta gurin gudun ceton rai ,   Saitin inda take jin tashin tv ta maida hankalin ta kafin ta ce    Hajja waye ne soja ? Shi baban jaririyar taki , Gwalalo idanu tayi   Soja ne daman ? Soja masu ƴaki da bindiga da jirgin ƴaki hajja ? Au daman baki ma san irin aikin mijin naki ba ? Hunm abun naki sai ido , bebiya ta auri makaɗi , Shiru falmata tayi tana jin wani tsoron sa sabo dal yana ɗarsuwa a ran ta , baban baby SOJA ne ?, " **** La'asar tayi musu a gidan da yake matsayin na biyamuradi youssouf da falmata , sojan da ya kawo su niamey shine ya je ya ɗauko su daga hotel ɗin ƙarƙashin umarnin youssouf da tun safe suke tare da maimartaba tare da wasu manyan ƙusoshin ƙasar a ainahin cikin gidan gwamnatin tarayya , Tunda suka shigo gidan da bayan sojan ya gama shigar musu da kayan ya danƙa ƴan mukullayen ga hajja me wurya ,   Santin gidan hajja take tana bin kowanne lungu da saƙo tana leƙawa tare da addu'o'i tana jere su iri iri , Gidan ba wani babba bane amma tsarin sa me kyau ne dai-dai da rayuwar mai rufin asiri kuma ƴan gayu , ɗakuna uku ne a cikin dan madaidaicin falon sai kuma kitchen da yake ta cikin falon sai keɓantatcen wajen cin abinci , ko'ina an sanya kayan da suka dace , cikin ɗakuna biyun gadaje ne iri ɗaya tare da wardrobe ɗin su,  sai dai ɗaya ɗakin akwai set ɗin gadon jarirai har da ƴar kwabet ɗin jera kayan jarirai da yake mallakin baby mama , gidan kam yayi kyau sai sa albarka hajja me wurya take , ita kaɗai ba tare da falmata ta kula ta tanka mata ba , yammaci lis biyamuradi Youssouf ya iso gidan tare da shi akwai sabon direban da gwamnati ta ba shi , bayan motar su cike taf da kayan abinci zuwa ƴan kananun kayan buƙatu na gida irin su , omo , sabulai , toothpaste d a sauran su,  Kai tsaye ya shiga gidan bayan ya ƙwanƙwasa ƙofa hajja ta buɗe masa , kan ɗaya daga cikin kujerun falon ya zauna bayan sun gaisa da hajja wacce take ta shi masa albarka har ma ta taya shi murnar ƙarin girman da ya ssmu wajen aiki , Dumm ! Yayi , ƙaƙa ankayi ta san an masa ƙarin girma ? Kamar ta san tunanin da yake cikin dariya tace ma sa    Ɗazu na gani a tv , gaskiya ɗan nan ka sha hotuna , anya hasken majigin hoto bai kashe ma karfin gani ba ? Yadda ka ƙware a rawar nan ta ku ta soji ka burgeni ai naso ita ma wannan matar ta ka tana gani ,da ta ga yadda kake shan juyi a fili nasan dole ka burge ta , hahaha Ɗan murmushi yarima yayi yana maida kallon sa ga falmata wacce take gefe a ƙasa riƙe da baby mama , alamun rashin kuzari duk sun bayyana agare ta ,    Fatima miƙo min ɗiyar ki na ga fuskar ta ko kouwa har yau kina mini rowar ta ne ?? Cikin sauri ta girgiza kan ta , "    Hajja miƙa ma sa ita ! Hajja me wurya ta karbi baby ta bashi ,   Ya karbe ta yana tambayar yanayin lafiyar jikin ta a yanzu ? Hajja ta amsa masa da samun tabbatuwar lafiya ga baby mama , ya shagaltu da yiwa ƴar sa wasa daga shi sai falmata da ke rakuɓe daga chan gefe , Hajja tana cikin kitchen tana aikin gyarawa tare da sanya duk wasu kayan abinci a inda suka dace , bata yi aune ba ta ji ƙarar bindigogi da sauti iri iri ya karaɗe falon da ya sa ta yunƙura da gudu tana neman wajen tsira , rashin sanin kan falon ya sa ta dunga cin karo da kujeru ,     Wani mummunan karo ta ci da doguwar kujerar falon da yasa tayi baya tare da sakin ihun da yasa biyamuradi miƙewa a zabari ya taro ta da hannun sa ɗaya , jin mutum a kusa da ita da ƙara kusantowar harbe harben da take ji ya sa ta ƙwaƙumewa a jikin sa ta zagaye dukkanin hannunwan ta biyu zuwa bayan sa , Hajja da ta fito da gudu saboda jin ihun falmata da ƙarar harbe-harben bindiga , sai ta ɗan yi turus tana yawo da ido neman bindigar take , Miƙa mata baby mama yayi ganin yadda take ƙoƙarin sanya kuka saboda ƙaƙƙarfar rungumar da falmata tayi masa ya sa ta firgita , Hajja ta karɓe ta tana cewa ƙarar bindiga nake ji ɗan nan ,  ince dai ba wai yaƙi aka soma ba ?? Bai amsa mata ba illa zaro wayar sa da yayi daga cikin aljihun sa bai duba waye ke ƙiran ba ya katse kiran ,   Hajja ku yi haƙuri sautin ƙiran téléphone ne hakka ba wani abou bane ya kai ga faruwa ba , Au to to , ai cewa nake yaƙin ne ya biyo mu har nan , ! Wucewa tayi da baby mama ɗaki tana neman abin goyo ,! Fatima    Sakar ni haka nan , na faɗi miki ƙarar talfo ne ...    Wayar sa da ta sake ɗaukar ruri ita ta sa falmata ƙara sanya ihu tana sake shigewa jikin sa idan banda ƙyarma babu abunda jikin ta ke yi , Sauri yayi ya ɗaga kiran ganin sunan me ƙiran na sa        princesse Allô ma jolie fille. Ya furta dai-dai lokacin da yake yin baya ya zauna akan kujerar da ya tashi tare da falmata wacce har lokacin riƙe take da shi tsam ta runtse idanun ta , Allo Mon amour ! tu me manques mon amour comment vas-tu aujourd'hui?   Gimbiyar maimouna ta amsa masa cikin salon sautin ta na gogaggun matan da suke tsakiyar ganiyar su , Je vais très bien et tu me manques aussi,      Ya amsa mata yana jin yadda daɗin sautin ta yake ratsa jikin sa ,         Ma princes , Albishirin ka ?    Tace da shi  . Ɗauke da amon murmushin da ya bayyana har a fuskar sa yace  ,    Gorro farare gimbiya ! Ko kassan yanzou jakka ( jakadiya )  ke sanar mouna saƙo ya taho dagga masarautar ku maigirma , ɗauke da gorron tsayar da ranar amren mu , gomma ga wata me kamawa , tabbas sa'a zata tabbata gare ni ranar da anka ɗamra amren mu da kai biyamuradin maraɗawa ! Wani irin daɗi ne marar misaltuwa ya ji yana ratsa zuciyar sa , tabbas zuciyar sa na ƙaunar maimounatu fiye da kowacce ɗiya mace , samun ta kuma nasara ce maigirma saboda a ta suffa da ƙawa tayiwa sauran mata zarra a wajen sa ,     Cikin shauƙi ya sake riƙe wayar sa da kyau yana ɗan bubbuga bayan falmata wacce ta fara dawowa hayyacin ta , da ɗayan hannun nasa , Wannan albishir naki mai girmou ne tauraruwar Agades , votre histoire a fait son chemin dans mon cœur, s’enfonçant dans mon âme. tamkar Falmata ta ji abunda ya faɗi , sai ta ɗago kan ta daga jikin sa , a hankali ta zare jikin ta daga nasa , ta miƙe tana taku sannu-sannu da ƙoƙarin barin falon , zuciyar ta shaƙare da haushin sa , ita shiyasa ta tsani soja , kome na su akwai sumfurin mugunta a ciki bayan haka tayaya sautin ƙiran waya da ta san ƴar ƙara ce mutane ke sawa a wayoyin su amma sai ga shi ta shi wayar ruwan alburusai take har da tashin boma bomai ," Cigaba yayi da hirar sa cikin nishaɗi yana jin yadda albishirin da tayi masa yake ƙara masa kuzari , lalle maimartaba yayi masa attaque par surprise       Fiye da mintoci ishirin suna hirar su sannan suka yi sallama ya aje wayar sa ,        Bankwana yayi da hajja wacce har lokacin tana kitchen goye da mama tana girka musu ɗan abinda zasu ci kafin kwanciyar bacci ,         Har ƙofa ta raka shi tana masa addu'a da godiya     Inda yake sanar da ita gobe zai wuce garin su zai iya kaiwa sati biyu zuwa kwanaki ishirin idan ya tafi saboda haka zuwa goben su masa lissafin abubuwan da zasu iya buƙata baki ɗaya ,     Bayan fitar sa ta kulle ƙofar ta dawo ciki zuciyar ta cike da wasi-wasi akan hirar da ta ji youssouf ɗin na yi da wata wacce bata kai ga sanin wacece ba , sai dai cikin hirar su da mafi yawa da faransanci shi youssouf ɗin yake bada amsa , ta fahimci mafi yawan maganganun nasa na soyayya ne saboda zaman da tayi a ƙasar kamaru , kurtun ɗan sanda ne mijin nata a bariki suka yi rayuwar su dan haka sosai take tsintar wasu kalmomin faransanci duk da dai shekaru ya sa ta manta yaren sosai ! A fahimtar ta youssouf yana da wata mace wacce yake tsanananin so da a kowanne lokaci zata iya cuso kan ta cikin rayuwar sa ta mallake shi wanda hakan yake babbar barazana ga rayuwar auren sa da yarinya falmata miskiniya ,    Hodijan ! Kai tsaye ɗakin da falmata ta shiga nan ta tasamma ,   A zaune ta tarar da falmatan daga ƙasa a bakin ƙofar ɗakin ta takure , Kallon ta tayi ta ji tausayin ta ya tsirga mata , hakkun ta fara hango ƙalubale a rayuwar auren yarinyar da ko fahimtar kalmar auren ma ba ta kai ga yi ba ,   mutuniyar kina zaune anan ne ?? da sauri falmata ta ɗago kan ta ,   Hajja ya tafi ??  Mama tana hannun ki ?    Eh ya tafi ga kuma mama a baya na , taso nan muyi wata magana kin ji ƙawalliye roman jaɓa ! ****** Abuja Nigeria Yakaka ta dage da neman ilmi tun ana koya mata haruffa ,A ,B,C,D , da kuma ا ب ،ت ،ث، sannu sannu ta haddace su tare da iya rubutun su , aka fara haɗa mata jimla , tana koyan rubutun su tare da sanin ma'anar su , ba ƙaramin daɗin koyar da yakaka malama maryam take ji ba saboda wankakkiyar ƙwaƙwalwa me saurin ɗauke abu da yakaka take da ita , A hankali ta fara lura da ƙarancin wayon da yake ga yakaka tare da gidadanci , sai tayi ƙoƙari tana gyara mata duk lokacin da ta ga tayi wani abunda bai kamata ba , tare da yawaita yi mata ƴan nasihu akan duk wasu manya da ƙananun zunubai . Gefe guda lubna na ƙara zage damtse ita a dole sai yakaka ta iya English da arabic ta iya magana da yarukan kamar yadda ta iya , dan haka sai ta tsiri yiwa yakaka magana da English ko Arabic ta daina yawan yi mata magana da hausa koyaushe , ga bangaren yakaka ita ma ƙwarai ƙwarai take jin daɗin haɗuwar ta da malama maryam da ƴaƴan ta , domin sun ja ta a jiki suna kuma gwada mata ƙauna hatta mahaifin su da ba sosai ma suke haɗuwa ba , amma duk lokacin da suka haɗu yana amsa gaisuwar ta faram-faram babu nuna tsangwama , Dan haka gidan su nan ne wajen yinin ta idan babu makaranta , ranakun makarantar ma daga ta baro makarantar gida zata tayi sallah ta ci abinci ta sauya uniform ɗin ta , ta dawo gidan ta kama musu ƴan aikace aikace kafin malama maryam tayi sallah ta ɗan huta , zaman ta da samy baby sai ya ƙaranta , Ranar wata litinin an tashi da hazo sosai tare da sanyi mai tsanani tun safe , zuwa yamma sai hazon ya ƙaru sararin samaniya yayi jawur iska me ƙura tare da tsananin sanyi yana kaɗa jikin al'umma , kusan kowa sauri-sauri yake ya gama abunda yake a titi ya koma gida Bayan tashin su yakaka a makaranta tare suka dawo da malama maryam ita ta wuce gida da zummar yin sallar la'asar ta ci abinci ta sauya kaya ta koma gidan malama maryam wacce ta sake jaddada mata kan lalle fa ta zo su yi darasi kar ganin yanayin garin ya sa ta ƙi zuwa , cikin ladabi ta amsa da    To zan zo Anty ! Da sallama ta tura ƙofar falon samy baby tare da danna kan ta kai tsaye , abunda ta gani ya sa jakar hannun ta saɓulewa zuwa ƙasa ,    Ɗaya daga cikin ƙawayen samy baby ne tare da saurayin ta suke yin masha'ar su nan kan kujerar falon babu kunyar ubangiji ko shakkar za'a iya shigowa agan su haka , Da sauri yakaka ta kawar da ganin ta daga kan su , tare da sunkuyawa ta ɗau jakar ta da sauri ta wuce ɗaki ba tare da ta sake kallon su ba tana jin yadda jikin ta baki ɗaya ya ɗau rawa da tasowar sabon yanayin da take ji cikin illahirin wata jijiyar jikin ta ," A kasalance ta gama kome hatta cin abincin ta da samy baby take ajiye mata shi a ɗakin ta, ta shiryo ta fito falon da fatan son sake ganin su , saboda ganin su na ɗazu da ya tayar mata da wani yanayi cikin jikin ta tare da bijiro mata da guguwar begen yarima da ta ɗan kwanta sakamakon mayar da hankalin ta da tayi kan karatu , sai dai ganin da ta yiwa waɗanan fasiƙan ya sa ta fara tuno da wasu abubuwa masu kamanceceniya da wanda ta ga suna aikatawa , da abunda ya shiga tsakanin ta da bature kam silum , ba ta tarar da su a falon ba , dan haka ta sanya ƙafafu ta bar gidan , tana tafe tana jin ƙewar bature kam silum na sake lulluɓar ta , ko yana ina yanzu ? Wataƙila ma ya manta da ita ! , ruwan hawaye ta ji suna taruwa a idanun ta ,daidai lokacin da take tura babbar ƙofar gidan su malama maryam ta shiga ,    karaf suka ci karo da lubna wacce take ƙoƙarin fitowa daga gidan hannun ta riƙe da wata leda , Yauwa ƙawata Dan Allah zo ki raka ni wancan gidan ummi ta aike ni ,    Tana mata nuni da wani babban gidan da yake chan kusa da ƙarshen layin su ,    Ba musu ta bi bayan ta , lokacin da lubnan take jan hannun ta ,    Saƙo lubna ta kaiwa matar gidan tana bata saƙon suka mata sallama suka yi fitowar su , Sun zo dai-dai tsakiyar harabar babban gidan , yakaka ta ga wani ɗan dogon saurayi ɗan gayu ya sha gaban lubna fuskar sa a marairaice idanun sa fes akan ta ,    Lubna Haba dan Allah ki saurareni , yau wajen watanni bakwai kenan ina bin ki da soyayya ta amma kina min walakanci , dan Allah ki TAIMAKA MIN ki yadda da soyayya ta wallahi ina tsananin son ki ,    Ba tare da lubna ta ɗaga ido ta dube shi ba ta kewaye shi ta wuce tana sake jan hannun yakaka , Charaf ! Ya riƙo hannun ta Lubna Dan Allah ki taimak....   Wani irin ƙara lubna ta sa kamar ya jona mata wuta , ta warce hannun ta da matuƙar ƙarfi cikin abinda bai wuci daƙiƙai ba ta cire hannun ta ta wanke shi da mari , kafin cikin muryar ta da take karkarwar kuka ta tace     Kar ka kuskura ka sake taɓa ni , ni ba ƴar iska karuwa ba ce ,    Kukan da ya zo mata ya sa ta kasa ƙarass zancen ta da gudun gaske ta juya tana barin gidan ,    Yakaka wacce take sakakai a tsaye ta bi shi da kallon tausayi a hankali ta furta kalmar     Kayi hakuri   Gƴaɗa mata kai yayi Cikin sanyin jiki ta juya ta bar shi a wajen ta nufi gida , Tana shiga cikin gidan ta tarar da lubna rungume jikin mamar ta banda kuka babu abunda take , malama maryam sai tambayar ta take me ya same ta ? Me aka mata ? Ta gaza bata amsa ,   Kallo mai bayyana haushi yakaka tayi mata lokacin da take zama a gefen malama maryam , Anty wai fa dan kawai wani mutum ya kama hannun ta yace ta taimaka masa yana son ta shine ta mare shi ta gudo gida tana wannan kukan ,    Ta ƙarasa zancen muryar ta na nuna jin haushin abunda lubna tayi ,     Waye ya kama hannun ta ? Wanne mutum ne , ke lubna ɗago ki dube ni waye ne ya riƙe miki hannu meye tsakanin ku da shi ? Ki faɗa min gaskiya ,    cikin shisshiƙar kuka lubna tace ummi , Mukhtar ne ɗan gidan Alhaji Umar , shine tun watannin baya yake tare ni yana cewa wai yana so na , shine yau ya tare ni a gidan su har ya riƙe min hannu wai na taimake shi yana so na ,     Nan take fushi mai tsanani ya bayyana a fuskar malama maryam , ta shiga yin faɗa meyasa tun ranar farko lubna bata sanar mata ba ? Ita kuma ta faɗawa baban su lubnar ya sami mahaifin yaron anyi musu tsakani ba ,     Faɗa take yiwa lubna tamkar zata doke ta , a karshe ta gargaɗe kan ko kusa ta da shi bata yadda ta sake tsayawa ba kuma zata faɗawa baban su ya sanar da mahaifin yaron su ja kunnen ɗan su , ya fitar harkar ƴar su ,   Sororo ! Yakaka tayi cikin jin mamakin malama maryam menene abun tashin hankali haka ?   Da son kwantar mata da hankali tace ,    Anty ai hannun ta fa kawai ya riƙe , kuma fa cewa yayi ta taimaka masa , wani irin kallo malama maryam tayi mata ,    Yakaka , Namiji baligi ya kama hannun mace baliga haramun ne a musulunci , muddin ba muharamman juna suke ba domin tafarki ne na samar da ZINA a tsakanin mace da namiji  , Zina kuma haramun ce a musulunci, kuma tana daga cikin manyan laifuka wanda ake kira Kaba'ir. Allah ya fada cikin Qur'ani و لا تقرب الزنى Wato kada a kusanci zina. Hikimar fadin hakan shine ba aikata zina kadai ba, aikata abunda zai janyo zinar irinsu rungumar juna , taɓe-taɓen juna da shafe-shafen jikin juna tsakanin namiji da mace dukkansu Allah yayi hani domin hanya ce ta kusanta kai ga zina , cikin sanyin murya yakaka tace Anty menene ZINA  ?? Zina ita ce Saduwa a tsakanin namiji da mace ,( ina nufin mace da namiji su kasance cikin abun rufuwa ɗaya jikin su na cikin na juna , azzakarin namiji yana cikin farjin mace ) ba tare da hukuncin aure ya shiga tsakanin su ba , duk mace da namijin da suka yi tarayya irin haka ba tare da an ɗaura musu aure kamar yadda addinin musulunci ya koyar ba to babu shakka sun aikata zina , kamar yadda na faɗa miki ita zina tana cikin manyan laifukan da Allah yayi hani da su sannan kuma ya tanadi hukunci ga duk waɗanda suka aikata ta , Hukuncin Zina a shari'ance ,  ita zina ba'a tabbatar wa da mutum ita dole sai da hujjoji, hujjoji guda biyu ne ko dai mutum ya yarda da kanshi ya aikata , ko kuma mutane huɗu su ganshi turmi da taɓarya a wannan hali ne ake tabbatar da zina, Amma ko mutune uku ne suka ce sun ganshi turmi da taɓarya sai ɗaya yace shi dai ya gansu a tube suna shafe shafe to baza a karbi shaidun su ba, za'ai musu bulalar ƙazafi tamanin tamanin , Amma idan shaidu sun kammala ko mutum ya amsa da bakin sa yayi zina Hukuncin sa a shari'ance shine bulala ɗari ga waɗanda basu taba aure ba. Kamar Yadda Allah ya faɗa" الزانية والزانى فاجلدا كل واحد منهما مأة جلدة، ولا تأخذكم بهما رأفة فى دين الله إن كنتم تؤمنون بالله واليوم الآخر. Wato mazinaci da mazinaciya ayi wa kowanne su bulala ɗari, kada tausayi ya kama masu dukan idan har sun kasance masu imani da Allah da ranar lahira. Sai wanda yayi aure akwai hadisin da yace duk mai aure ko wanda ya taɓa aure idan ya taɓa zina za'a jefe shi, amma sai idan shine da kanshi yazo yace yayi zina yana so a jefe shi, amma idan bai yadda a jefe shi ba ba za'ayi mishi dole ba za'a barshi ne. Wani irin tsoro da tashin hankali me tsanani ne ya dirar mata , cikin wata irin muryar da ke bayyana tsantsar firgicin da ruhin ta ke ciki , tace    Anty ko da mutum taimako yayi , Malama maryam cikin tsanaki tace ban fahimce ki ba yakaka wanne irin taimako ne yake zuwa ta hanyar aikata zina ?? Anty ina nufin ko shi namijin cewa yayi mace ta taimaka masa , sai ita ma ta taimaka masa , suka yi , shikenan tayi zina ?? Su dukan su sun aikata zina , saboda babu biyayya ko temakekeniya tsakanin bayin Allah wajen saɓa masa , su dukkanin su basu da hujjar kare kan su , suyi gaggawar tuba ga ubangiji domin zina babbar musiba ce , Sannan kuma yakaka ai duk namijin da zai cewa mace ta taimaka masa ta bashi kan ta suyi zina , ai wannan babban maƙiyi ne a gare ta , bata da maƙiyi sama da shi , mugu ne kuma macuci domin na farko zai ɓata tsakanin ta da ubangiji , yasa ta aikata abunda Allah zai yi fushi da ita , da zai hana ta samun ganin Alkhairi da dacewa cikin rayuwar ta duniya da lahira har sai idan ta tuba , Na biyu duk ranar da mutane suka san me suke aikatawa, mutanen kirki zasu guje ta , za'a dunga mata kallon fasiƙa, mazinaciya ƴar iska , karuwa . Na uku idan ta hanyar zina da suka aikata ta samu ciki ta haihu , abun da ta haifa idan ya girma shi ma da kan sa zai tsane ta , ƙimar ta zata zube a idanun abunda ta haifa , saboda ta zamto sanadin da mutane zasu dunga ƙyamatar sa da ganin sa wani mutum da aka samar da shi ta haramtatciyar hanya , Bayan haka illolin zina suna da yawa , daga ciki akwai ɗaukar munanan cututtuka da zasu iya kai me su ga mutuwa , A ƙarshe namijin da duk zai yi zina da mace abu ne me wuya ya aure ta , ko da ya aure ta kuma bazai taɓa ganin ƙimar ta da mutuncin ta ba , sannan ƙanƙanin kuskure zai iya haifar da zargi a tsakanin su da zai lalata musu aure , Kuma duk macen da tayi zina kafin tayi aure bata da wata martaba a idanun duk wani namijin da zai zo ya aure daga baya saboda ta rasa ƙima da mutuncin ta na ƴa mace tunda tayi zina . Ki gujewa abunda duk zai kai ki ga aikata ZINA yakaka cikin ta akwai tarin masifu kin ji ko ?? Bata amsa ba illa miƙewar da tayi bata tsaya ba ta taka da gudun gaske tana barin gidan ba ta ko tsaya ta sanya takalman ta ba bare ta saurari ƙiran da malama maryam take mata , gudu take bata ko dub Inda take jefa ƙafar ta ,    Da ƙarfi ta tura ƙofar ɗakin tana shiga ta zuɓe a tsakiyar ɗakin tana sakin wani irin kuka marar sauti da yake tuƙowa daga ƙasan ruhin ta ,    Cikin wata irin murya ta fisgo kalmar ,    ALLAH NA TUBA , NA TUBA ALLAH , BAZAN SAKE BA ,ALLAH NA TUBA KA YAFE MIN ,   Kuka take tana maimaita kalmomin nan jikin ta har tsuma yake , Ashe haka ne girman laifin da ta aikata batare da ta sani ba ? Ashe ita ɗin me tarin zunubi ce ? Ashe baza ta samu wani alkhairi ba arayuwar ta tunda tayi zina , Ta jima a zaune a wajen tana kuka har duhun dare ya shigo , zuciyar ta ta tsorata iyaka , neman yadda zata yi Allah ya yafe mata take yi , sai dai bata san yadda zata yi Allah ya karbi tuban ta ba , ji take kamar zata mutu , Tashi ta sake yi tana gama hanya saboda kukan da ta ɗauki lokaci tana yi yasa kan ta sarawa tare da fara jin jiri , tana gama hanya ta fito , bata ko dubi ɗakin samy baɓy da kiɗa ke tasowa ta cikin sa alamun da ke nuna ta dawo gidan ba , ta sake fita , hanyar gidan malama maryam ta sake  ɗauka ,   tana so ta san yadda zata yi Allah ya yafe mata , tana so ta san yadda zata yi ta gyara kuskuren ta , a falo ta tarar da malama maryam tare da iyalan ta suna cin abincin su na dare ,    Babu sallama ta rakaɓe daga bakin ƙofar gami da sakin kuka me ciwo , hankali tashe malama maryam ta tsame hannun ta daga abincin da suke ci ta miƙe , ta zo ta kama yakaka ,     Tambayar ta take lafiya ?meye ya same ta ? Ko wani abu ya samu antyn ta ? Daman yanzu take so idan ta gama cin abinci lubna ta raka ta gidan nasu ta duba ta domin ɗazu ta fita bata cikin nutsuwar ta yanzu kuma ta dawo tana kuka , shin menene yake damun ta ??      Cikin muryar ta da kuka ya fara disarwa , tace nayi ZINA malama maryam , ki taimake ni ki faɗa min yadda zan yi Allah ya yafe min , ban sani ba malama maryam wallahi ban sani ba ,   Ta shi , ta shi mu shiga ɗaki ki nutsu ki min bayani yadda zan fahimce ki ,    Ta kama hannun ta zuwa ɗaki ta zaunar ta bakin gado , ina sauraran ki me kike son faɗa min yakaka ? Tiryan tiryan , yakaka ta fara bada labarin tun daga farkon haɗuwar ta da yarima har yanayin yadda abubuwa suka kasance har zuwa yadda alaƙar ta da samy baby da yadda ta yaudare ta ta zo da ita garin  abuja ta baro ɗanyar jaririyar ta tare da makauniyar ƙanwar ta,  bata idasa ba malama maryam ta katse ta , Kin yi kuskure yakaka , kin yi kuskure , kin yi kuskure ,! Kaicho       wani irin tausayi chakuɗe da bacin rai take ji cikin ran ta , tamkar wata makusanciya a gareta ce ta aikata abubuwan da yakaka ta aikata , tun farkon fara koyar da yarinyar ta fahimcin tana da raunin sani sosai da sosai game da addini , kusan ma bata san kome ba , shiyasa ta ɗaura aniyar ganin ta kawo sauyi ta fidda ta daga duhun jahilci , cikin rashin sanin ta ashe jahilci tare da rashin wayon yarinyar har ya kai haka ( Bata san menene zina ba ) ? Ta yadda aka yi amfani da jihilcin aka cutar da ita cuta mai tsanani irin haka ? Kukan da yakaka take ya tsansnta ganin shirun malama falmata ya ɗau lokaci tare da bayyanuwar matsanancin tashin hankali bisa fuskar ta ,   ALLAH zai yafe miki yakaka , muddin kika nemi yafiyar sa tare da niyyar baza ki sake komawa ga aikata saɓo irin wannan ba , ALLAH me yawan gafara ne ga bayin sa , Duk da cewa akwai bayanai daga malamai game da mutumin da ya aikata saɓon Allah alhalin bai san cewa sabon nan me girma bane da zai iya kai me shi ga shiga wuta ,ko kuwa bai ma san saɓo bane baki ɗaya, akwai hukunce hukunce , hukunci na farko shine , Shi JAHILCI ba'a uzuri da shi, sai dai cikin wannan hukuncin akwai bayanai da suke nuna akan karbi uzurin JAHILI , idan ya kasance gurin da ka tashi babu addini , babu malamai masu koyarwa ,ko kuwa an hana ka damar fita neman ilmin kuma ba'a koyar da kai ba a gida ,  to za'a iya yi maka uzuri da wannan , amma idan gurin da kake akwai addini akwai malumma , sai kaƙi fita ka nemi ilmi kasan hukunce hukuncen addini kayi zaman ka cikin jahilci to wannan baka da uzuri a addini , jahilcin ka ba uzuri bane , to amma idan ka rasa damar samun ilmi ne , akwai hadisin manzon Allah sallalahu alaihi wa sallam da yake cewa :      Allah ya ƙetarar da Al'umma ta abu uku , ma'ana ya yi musu afuwa akan abu uku , na farko shine mutum yayi abu cikin rashin sani , na biyu mutumin da ya aikata wani kuskure akan mantuwa , sai na uku wanda aka tilasta ma sa aikata saɓo, ! To idan aka yi duba ga wannan hadisin za'a yiwa mutumin da duk ya aikata wani saɓo cikin rashin sani , uziri a sassauta masa , sannan shi kuma yayi tuba zuwa ga Allah , tsarkakaken tuba , Manzon Allah yana cewa : duk wanda yayi tuba na gaskiya to zai kasance kamar bai taɓa aikata wannan Zunubin ba , amma wanda yake tuba alhali yana komawa ga aikata zunubin sa to tamkar yana yiwa Allah izgili ne . kiyi Tuba na gaskiya yakaka tare da niyyar baza ki sake kusanta kan ki ga aikata ZINA ba a rayuwar ki , Allah zai yafe miki ya wanke ki a idanun Al'umma domin Laifin shi kika yiwa , Sannan , ki tashi ki nemi ilmi ki kuma yi aiki da shi idan dama ta samu gare ki kome ƙanƙantar sa ki koyar da ilmin da yake gare ki domin sauran Al'umma su amfana , shiriya ta zo miki hasken ilmi ya zo miki ki sa hannu biyu ki karɓe su ƙwarai akwai falala tare da samun dacewa a cikin su , ki manta da rayuwar baya ki himmantu wajen neman gafarar ubangiji akan saɓon da kika wanzu kina aikatawa , da fatan kin fahimce ni ?? bata amsa ba illa hannu da ta kai ta rungume malama maryam , idanun ta na zubar ƙwallar da ita kaɗai ta san dalilin sauƙar su a daidai wannan lokacin Godiya ta dunga jerowa malama maryam har lokacin da ta sanya ƙafar ta tana barin gidan lokacin dare ya fara shiga karfe goma saura , kan titi babu kowa garin ya sake ɗaukar sanyi , a hankali take tafe iska yana ɗaga hijabin ta , tayi zurfi cikin tunani , daki-daki take tuno kome da ya dunga faruwa a rayuwar su ita da ƙanwar ta , tana so ta zargi iyayen su akan killace su a gida da suka yi suka hana su neman ilmi , sai dai so irin na tsakanin ɗa da iyayen sa ya mata dabaibaiyi yaƙi bata dama , ji take suna da wata hujjar su , babu shakka akwai dalili , tunanin falmata da baby mama yayi mata dirar mikiya , wata irin kunyar falmata ta ji tana nuƙurƙusar ta , yaya zata Ji ranar da duk ta san irin kuskuren da tayi har ta samar da baby mama ta gudu ta bar mata ita ? Wataƙila daga ranar zata fara tsanar ta , tsoro take ji tsoron girma ya zowa baby mama ta samu sani akan irin ta hanyar da aka samar da ita , ? Me zata cewa waɗannan bayin Allah biyu ?? Lalle wajibi ne a gare ta ta nemi ilmin addini ko domin ta samun ƙarfin guiwar da zata iya fuskantar su tare da tarin hujjoji da bayanan da addinin ya tanadar domin ta gamsar da su ta kuma wanke kan ta a idanun su su san cewa ta aikata kome ne cikin DUHUN JAHILCI ,! Ko zasu fahimce ta ? Ko falmata zata yadda ta cigaba da riƙe ta a matsayin ƴar uwa masoyiya ? Ko baby mama zata yadda da ita a matsayin uwa ?? Yaushe wannan ranar zata zo ? Zata zo nan kurkusa , ko sai bayan shuɗewar tsawon wani lokaci ? Abun da ta riga ta sani muddin su na raye wannan ranar zata zo , YARIMAN MARAƊI , Zuciyar ta ta auno mata da sunan sa da kome da ya wakana cikin rayuwar ta a wannan gaɓar shine sanadi , bata gan shi ko kusa tare da duhun jahilci makamancin nata ba , kome da shi yayi mata yayi ne cikin ilmin sa ,da sanin sa ya aikata Zina da ita , zuciyar ta take ji tana wani irin buɗawa da sabon yanayin da yake shigar ta akan sa da sabon matsayin da ya kamata ta ajiye shi tun farko a ran ta , Tunowa ta fara yi filla filla da farkon haɗuwar su har zuwa ranar ƙarshe da ya kore ta daga motar sa a tsakiyar titi  tana kuka , yayi tafiyar sa ya bar ta har yau bai sake waiwaiyar ta ba , tabbas shi macuci ne azzalumi agare ta bai chanchanta da samun soyayyar ta ba ko kaɗan , bai taɓa son ta ba , kawai amfani yayi da jahilcin ta ya ribaci gangar jikin ta ya yasar da ita tare da cikin da yayi mata , wani irin yanayi mai ƙarfi da kaifi ta ji yana keta zuciyar ta a game da shi , hannun ta ta kai ta tattaro bakin hijabin ta ta riƙe tare da cije gefen leɓen ta na ƙasa da ya zo daidai da zubowar hawayen ta da yake nuni da mummunan ƘULLACIN da tayi masa .... !!!!!! [9/3, 10:13 PM] +234 806 122 1116: Fikrah writers association MAFARI ( Hargitsin Rayuwa ) umm'muaz 31 Ba ƙaramin kaɗuwa Youssouf ya yi ba lokacin da Maimartaba yake shaida masa zancen auren sa da Siyama , da har an riga an miƙa dukiyar auren ta ga mahaifin ta dake niamey , za'a yi ɗaurin auren sa da ƴan matan duk biyu a rana guda kamar yadda ya buƙata , Ya jima a zaune gaban Maimartaba yana jin yadda zuciyar sa take cunkushewa da tarin takaici , Ba tun yau ba ya gama lura da take-taken yarinyar , shi yasa sam baya sakar mata fuska ashe bai sani ba har tayi girman da zata iya yin tsaurin ido irin haka a matsayin ta na mace ta doshi iyayen sa da buƙatar son a haɗa su aure ? Babu shakka zata ɗanɗani kuɗar ta a hannun sa , sai tayi danasanin wannan mummunan shisshigi da tayi ta kutso kan ta cikin rayuwar sa da take a hargitse a halin yanzu , Ganin shirun sa ya tsawaita ba tare da ya amsa da amincewar auren ba , ya sa me maimartaba yin gyaran murya   Da fatan ba zaka bijirewa oumarnin mu ba ? Bisa ga wannan haɗi da munka yi na amre tsakanin ka da ƴar ouwar ka , saboda ba muyi haka ba face sai da munka hango tarin alkhaire tare da dacewa sannan munka so ƙulla igiyar amre a tsakankanin ku , wannan ɗiya ɗiyar ƴar uwa ta ce , kai ma kuma ƴar ouwa take gare ka , ina yi maka oumarni ka karɓi amren nan da hannu biyu da ikon Allah gaba kai zaka yi farin ciki . Kalmar 'Umarni, ta daƙile dukkanin wani yunƙuri da zai iya yi , domin shi ɗin me yawan biyayya ne ga iyayen sa , haɗi da sanin da yayi a yanzu shi me tarin laifuka ne , wanda yake neman wata kafa ko yaya ne da zai iya faranta ran iyayen sa ta dalilin ta, ko domin su iya masa uzuri a duk ranar da laifukan sa suka bayyana a gare su , su duba irin faranta mu su da yayi su sassauta masa hukunci , Cikin harhaɗa kalmomin da suke suɓcewa daga harshen sa saboda kaifin su da yake iya ji ya furta , Na Amince , Allah shi ƙara girma da ɗaukaka . Da murmushi bisa fuskar sa yace Madallah da kai , Allah shi maka Albarka , Ya Albarkaci zuri'ar ka , Allah shi yi katanga tsakanin ka da miƙiya , kana iya tafiya ka fara shiri doumin nan da sati biyu da ranar tayi dai-dai da gomma ga watan gobe ake ɗaurin amre . Godiya yayi ya miƙe yana barin shigifar sarki , kai tsaye gidan da zai tarar da Tafeeda ya nufa , Cikin sa'a ya same shi dawowar sa kenan daga aiki da sanyin la'asar , Babu walwala a fuskar sa ya samu wajen zama bisa kujerun shan iska ,   Ɗan ouwa ka kuwa san me ke shirin farouwa gare ni ? Maida ganin sa yayi kan sa , bayan ya miƙa masa sassanyan lemun da ya tsiyayo masa a kofin gilashi , Sanar da ni ɗan ouwa Wai amren mataye biyu a rana gouda , kuma amre tare da yarinyar nan siyama da ko ƙamnar duban ta bana yi , shin baka yi tounanin akwai wani dalili da ya sa maimartaba haɗa min amren mataye biyu a rana gouda ba ?     Ɗan guntun murmushi tafeeda yayi Banda abun ka Yarima shin amren mataye biyu a rana gouda ba gata bane ?    Ita siyama ai duk inda ake neman macen amre ta zarta ,   Maimartaba bashi da sani kan kome wataƙila hasashe ne yayi irin nasu na manya ya sanya shi yi maka gatan amra maka mataye biyu a rana gouda , Juyar da kan sa gefe yayi yana jin yadda ran sa ke sake ɓaci , kan batun auren , ga kuma ya lura Tafeeda ba shi da niyyar taya shi jimami , shi ina zai kai mata har uku a shekarun nan nasa ??     Kurɓar lemun sa tafeeda yake yi yana satar kallon youssouf da yayi tagumi hannu biyu ya nisa cikin tunani ,    So yake ya masa tambaya game da al'amuran sa na ƙasar nigeria , ɗiyar sa da take can , ƙaƙa ya ƙarƙare da barin ta a chan ? Hannun wa ya baro ta ? Sai dai rashin son tuno masa da ita ya sanya shi haɗiye tambayoyin sa , ga zaton sa Biyamuradi yayi amfani da shawarwarin sa , ya baro duk wasu kuskuren da ya aikata a inda ya aikata su ! Farin cikin da Siyama ta tsinci kan ta cikin sa bai misaltuwa , domin duk wani da ke mu'amala ta kusa ko ta nesa da ita zai iya shaida farin cikin tare da walwalar da ke tare da ita , da ɗai bata taɓa farin ciki me yawan haka ba cikin rayuwar ta ,    Ƙulluwar aure a tsakanin ta da Youssouf wani abu ne da tayi shekaru tana mafarkin sa a bacci ko a farke , bata taɓa zaton zata samu damar mallaƙar sa a matsayin miji a sauƙaƙe haka ba , a kuma daidai lokacin da take zaton ya sulluɓe mata zai zama malakin wata ba ita ba , duk tunanin ta na bata sai wani nisan shekaru wataƙila idan da rabo suyi aure , ga haɓakar farin cikin ta ashe tabbatuwar mafarkin ta zuwa gaske yana kurkusa , ashe tare zasu mallake shi ita da wacce take tunanin ta fita sa'a , ashe sa'ar na gare ne su biyu ,? Bata ji ko ɗar ba akan sanin da tayi auren su auren haɗin iyaye ne , tare da sanin da take da shi akan irin tsanar da shi yake gwada mata , ta ji ta gani ta amince ta kuma shirya yin zaman aure da shi da gasken gaske , cikin kowanne irin hali , tana jin son da ita take masa zai ishe su rayuwa ita da shi ,    Soyayyar sa ga gimbiya maimouna bata razana ta , illa kishi da ke nuƙurƙusa ran ta , dan haka ta sha alwashin ko da ƙaƙa , sai sun raba soyayyar youssouf biyu ita da maimouna kamar yadda zasu mallake shi a matsayin miji su biyu a lokaci guda , idan ya so ita na ta kason soyayyar idan ya so ya zubda a rariya , bata da damuwa son da take yi masa ya ishe su , . Shiri take ka'in da na'in ubbo tana taya ta haiƙan , gefe guda hajiya umma na bada ta ta gudummawar a matsayin siyama na ɗiya a gare ta , ɗiyar da ta goya tayi rainon ta tun tana tsumman goyo , Lokacin da gnala take sanar da gimbiya maimuna dangantakar dake tsakanin youssouf da siyama har ma da zantukan da ta ji siyama na tattaunawa da  ubbo , bata wani ɗau batun da muhimmanci ba , saboda wasu dalilai nata da take ganin ko da ace zai aure su su biyun ita bata jin hakan zai dame ta , burin ta ɗaya tal , shine ta samu nasarar aiwatar da ƙudurin da zai sa ta aure shi . Dan haka ko da yake kame-kamen sanar da ita batun auren sa da siyamar yana bin ta da kalaman rarrashi , kwantar da murya tayi ta dunga zuba masa sassanyan rikicin da ya sake ɗaga darajar ta a idanun sa tare da sake dilmiyar da shi cikin ƙaunar ta ,      Ya dunga jin yayi sa'ar samun nutsattsiyar mace kuma me haƙuri, wacce mace ce a zamanin yanzu da za'a yiwa kishiya gab da lokacin auren ta , a kuma haɗa su aure rana guda , ba'a yi danbarwa da ita ba ? Ƙwarai ƙwarai maimouna ta ƙara ƙima a idanun sa , Samun haɗin kan ta farad ɗaya ya lafa guguwar ƙin auren a cikin ran sa , sai ya samu nutsuwar fuskantar shirye-shiryen auren tare da cigaba da zarya wajen sabon gurin aikin sa da aka tura shi Dosso , inda zai zama shugaban soji na baki ɗayan yankin na jahar Dosso , Tafkeken gida aka mallaka masa tare da motocin hawa biyu , ƙari da tarin hadimai sojoji tun daga kan masu gadi , direba , har zuwa kan me girki . Tsakanin jahar Maraɗi da jahar Dosso babu tazara me yawa , dan haka lokacin da yake da samun tabbacin wajen zama a dosso , sai yayi niyyar bayan bikin su , zai dawo da gimbiya maimouna nan gidan sa na dosso , kusa da shi , ita kuwa siyama ta cigaba da zama can a maraɗi , tunda ita ta zaɓi auren cikin gida sai ta samu matabbata a cikin gidan , ! Sai dai yana sanar da hajiya umma niyyar sa , a take ya ga sauyin fuskar ta ,      Abu guda ta ce da shi . Kome tsanani kayi ƙoƙarin kwatanta adalci tsakankanin matayen da Allah ya baka amanar riƙon amren su , kar ka kuskura ka karkata ga ɗaya daga cikin su , saboda gujewa fushin Allah da azabar sa ka kiyaye , siyama da maimouna duk su biyun matan amren ka ne . ***** Tun farkon satin aka fara gudanar da shagulgula da wasannin daga bangaren masarautar maraɗi har da ta Agades wanda suke da tarin wasannani da al'adun gargajiya fiye da na maraɗi , haɗi da shiri sosai da suka yi na bikin kasantuwar kowa ya san gimbiya maimouna ɗiyar gata ce ta sosai , Har zuwa yau da take ranar sakun lalle ga amare , gobe juma'a za'a ɗaura auren Kamar yadda al'adar masarautar maraɗi take , duk lokacin da za'a yi sakun lalle ba'a yi a cikin masarauta , can tsibirin maraɗi ake tafiya da amayar ,"wani ƙaramin gari ne da yake ƙarƙashin jahar maraɗi da ake ƙiran sa tsibiri bashi da nisa sosai da ainahin cikin garin maraɗi , Gidan sarkin tsibirin nan ake sakun lallen a cikin gidan akwai wata mace da ake ƙira ,inna , wacce sunan sarautar ta ce ,inna ɗin ," ita take sakun lalle ga amaren da duk za'a shigar ko za'a fitar daga masarautar maraɗi, Karfe ɗaya na rana gimbiya maimouna tare da ƙanwar mahaifiyar ta da ƙanwar mahaifin ta da matar maimartaba sarkin agades ta biyu tare da wasu daga cikin matan ƴan uwa na ƙurƙusa tare da rakiyar amintattun hadiman ta mata biyu da bayu maza uku  sai kuma ƙaramar jakaɗiyar agades,  jirgin su ya iso tashar jirgin sama na maraɗi daga agades ,inda nan take motocin da suke jiran su domin kai su tsibiri suka ɗauke su kai tsaye zuwa tsibirin maradi , Tarɓa me cike da girmamawa aka yi musu , inda suka tarar da gidan cike da manyan mata masu sarauta na kurkusa da fada cikin su har da manyan yayun biyamuradi ,"Ammi da Dada da Asma'u da ake ƙira ma'u ƴar wajen hajiya mama ta farko . ," da kuma ƙaramar jakadiya . Tsakanin su bai cika awanni biyu ba siyama ta iso ƙarƙashin rakiyar ƙannen maimartaba sarkin maraɗi su biyu tare da hajiya mama da ubbo sai kuma ƙannen baban ta su biyu , Ta ko'ina buɗa da ƙirari ne yake tashi saboda makaɗa da maroƙa da suka cika faɗar sarkin tsibiri duk da cewa an dakatar da su daga shiga cikin gidan inda aka fara shirin sakun lallen amaren       Shimfiɗa ce aka yi da manyan jajayen dardumai , a tsakiyar babban ɗakin , inda aka ajiye babban tum-tum na zama a tsakiyar shimfiɗar , Inna tayi umarni da a shigo da siyama za'a sanya ta a lalle , Ko kafin bangaren gimbiya maimouna su ce kome , hajiya mama ta yunƙuro ,   Wacce siyama kouwa ? Ai ita maimouna ita ce matar farko dan haka ita za'a fara sanyawa ga lalle ko kouwa ?   Hakka zance yake ranki ya dade uwagijiya ta ,   cewar ƙaramar jakadiyar Maraɗi Aiyuriyuriyyyy ayuririyyyyyy ayyuririyyyy !! Wata zazzaƙar guɗa ta fito daga hancin jakaɗiyar agades , saboda jin babban matsayin da uwargiyar su ta samu ,   Taka a sannou-sannou ƴar sarki jikar sarki , matar yarima ɗan sarki surikar sarki , gaban ki salama bayan ki lafiya  farar macce fitila gida , tauraruowar ki me ƙarfi ce wacce hasken ta ya tarwatsa ya zagaya nahiya tun dagga birnin agades har yankin maraɗi , wouce gabba kin yiwa sauran mata zarra , kin yi gado ba haye kika yi ba mahaifiyar ki ai ita shugaba ta matayen agades ,     A hankali ta sanya kan ta cikin ɗakin tana jin yadda ginshiri irin na sarauta yake sanya ta ƙasaita da jin faɗi. Bayan shigar ta guda daga bangaren mahaifin ta tare da guda daga bangaren mahaifiyar ta suka rufa mata baya , ubbo ta yunƙura zata shiga hajiya mama ta dakatar da ita tare da yiwa ma'u umarni da ta bisu kamar yadda al'adar take mutum ɗaya daga bangaren dangin miji ke shiga ɗakin sakun lallen . Bayan zaman gimbiya maimouna inna ta janye hular alkƴabbar dake bisa kan ta , baƙin gashin ta da ya sha gyara ya bayyana , inna ta sanya wata ƴar kyakkyawar kibiyar kitso ta raba gashin biyu hagu da dama , Matar da take waziriyar inna ta miƙo mata wani ƙoƙo cike fal da madara sanuwa/nono , ta karkata ƙoƙon a sannu sannu ta fara zuba madarar a daidai tsakiyar tsagun , A hankali kakkauran nonon ya fara kwaranya , bisa tsagun kafin ya saki layi ya tarwatse a gaba ɗayan cikin gashin maimakon ya bi kan hanyar da aka masa ƙaɗai , Nan take inna da waziriyar ta suka haɗa ido suna masu gƴaɗa kai a hankali , yayin da fuskar ma'u ta sauya tana bayyana ɓacin rai a sarari , har aka gama zuba nono nan haka yayi faca-faca akan fuska da jikin kayan gimbiya maimouna , A fusace ma'u ta juya ta fita daga ɗakin gefen mahaifiyar ta ta je ta tsugunna ta mata raɗa , nan take fuskar hajiya mama ya bayyana wani sirrantatcen murmushi , kafin tayi gyran murya tayi wa jakadiya alama da ido , Nan take jeka ta karkace kai ta rangaɗa ƙaƙƙarfar guɗa da ta sanya , mutanen agades samun kwanciyar hankali musamman innonin gimbiya maimouna da duk suka sha jinin jikin su , kan shirun da suka ji daga ɗakin ko dai ƴar ta su tayi kuskure ne cikin rayuwar ta ? Amma jin buɗa daga bakin jekadiyar maraɗi ya sa hankalun su ya kwanta yayin da tasu jakadiyar ma ta karkace kai ta dunga sakin zaƙaƙan buɗoɗi ,   Bayu mata biyu suka jawo wata ɗirkekiyar tunkiya fara sol suka ɗanka ta ga hannun matar sarkin agades ,    Tunkiyar gimbiya maimouna ce ta sakun lalle , nan take bayun agades suka kama igiyar tunkiyar suka riƙe gam . Ma'u ta koma ɗakin ƙarƙashin umarnin hajiya mama ta sanya farin kyalen ta share fuskar gimbiya maimouna gami da jan hular alkyabbar ta ta rufa mata akan ta , Suka fito daga ɗakin , Bayan an sauya shinfiɗa da wajen zama aka yi umarni a shiga da siyama , Ƙanwar mahaifin ta ɗaya tare da hajiya mama sai kuma ubbo su ne suka shiga da ita ta zauna akan tum-tum Inna ta tsaga gashin ta , ta karbi ƙoƙon madarar ta shiga tsiyayo mata shi daga tsakiyar kan ta sannu sannu ya shiga bin layin yana gangarawa har zuwa kan siririn karan hancin ta yana ɗiga a gaban rigar ta , har nono ya ƙare bai karkace hanya ba , Wata ƙarƙarfa guɗa ce ta taso daga hancin inna da tayi amsa kuwwa har fada da nan take makaɗa suka ƙara ƙarfin kiɗan su da ƙirari , Daga waje ma bayun masarautar maraɗi suka dunga sakin buɗa ba ƙaƙƙautawa , Zuciyar hajiya mama tayi bakikkirin lokacin da ubbo ta sunkuya ta ɗau farin kƴallen tana gogewa siyamar madarar fuskar ta idanun su suka gauraye cikin na juna sassanyar ƙaunar da take tsakanin su tayi tasiri idanun siyama suka ciko da ƙwallar murnar ganin wannan ranar me cike da ɗinbin tarihi a wajen ta , a hankali ubbo ta kai hannun ta duk biyu ta rungumo siyamar zuwa jikin ta , a hankali ta raɗa mata a kunne    Madallah da ke ƙauna ta ɗiyar kirki , me daraja ,Madallah da ke mace tagari abar alfaharin iyayen ta da mijin auren ta ! Ko kusa ran hajiya mama bai yi daɗi ba da cikar budurci da alamu suka bayyana ga siyamar kamar yadda al'adar daman take nuni ne da macen da take cikakkiyar budurwa ita ce wacce nonon ke bin dai-dai tsagun layin ba tare da ya karkace ba , ta so ƙwarai ace an samu matsala irin wacce aka samu ga gimbiya maimouna , domin tayi amfani da damar wajen hana yiwuwar auren siyama da youssouf wanda ta ji zancen sama ta ka babu zaton ta babu tsammani , kuma a zahiri bata ƙaunar duk wani abu na alkhairi ya raɓi youssouf , Sannan irin tashin hankalin da mommoudu ya shiga da jin zancen haɗin amre tsakanin youssouf da siyama , alhalin shi zuciyar sa ta rayu tsawon lokaci ɗauke da dakon soyayyar siyamar , meyasa kome na cigaba da samun nasarar rayuwa yana ga youssouf ba shi ba ? Meyasa maimartaba ya tattara duk wasu gata da kulawa ya bada ga youssouf alhalin ga shi , shine kuma ƙarami ? ******* Biki aka yi na bajinta da gata , irin wanda ba'a taɓa yin makamamcin sa ba a tsakanin jahohin biyu , aka yi biki aka gama lafiya lau amare sun ka tare a gidajen su da suke cikin da'ira guda sai dai kowaccen su tana sashin ta yayin da sashin biyamuradi yake tsakiyar nasu , gini ne guda uku a tsaye , Daren ranar lahaɗi da aka yi wuni aka watse shine daren da farkon sa yake zaƙi ga youssouf kafin zuwan tsakiyar sa da kome ya rikiɗe ya kuma sauya ya birkice ya hautsine masa , ya sanya shi shiga ruɗani , nadama bakin ciki tare da tarin tsoro , Maimouna ita ce macen da ya ɗau aniyar kwada mata ƙauna da soyayya irin wacce yake da burin nunawa ga matar auren sa , hakan kuma ya fara gwada mata a tun farkon daren da yake jin tamkar ya haɗiye ta dan so ko kuwa ya buɗe cikin ƙirjin sa ya cusa ta , sai juyi da ita yake yi yana lallaɓa ta daki-daki tamkar ƙwai , kafin kome ya kankama , zuwa lokacin da zai fahimci bara gurbin ƙwan da ya ɗaukowa kan sa ya kuma ta'alaka soyayyar sa akan ta , har ma ya sallama mata duk wani so gami da yadda da ya mallaka , Ashe yayi kuskure ne , shin ashe ta riga ta so wanin sa kafin shi ? Har ma ta mallaka masa abu mafi daraja agare ta wato gangar jikin ta ? Ashe ita ɗin ta ha'ince shi ne ? Shin ko dai shine ya ha'inci kan sa ? Shin ko dai ayar Ubangiji ce ke tabbata akan sa ? Idan kayi zina da matar wani ? Idan kayi zina da ƴar wani ?  Idan kayi zina da ƙanwar wani ?? Uwar wani ?? Tunanin hakan ya tsorata shi tsoro me tsanani , da ya hana tasirin fushin sa bayyana har ya nuna shi ga gimbiya maimouna da ta cigaba da yi masa lamɓo da nuna masa salo salo na gogaggun mata har da ƴan ƙananun koke koken ta , ita ciwo take ji , Sai yayi wani zugum kamar soko ya sanya mata ido , ah to shi zata yi wa bariki ?? Ai ya san me ake nufi da budurci , " amma tunaninikan da suke bijiro masa da shuɗaɗɗen laifin sa suke barazana ga nutsuwar sa saboda zuwan dodo-dodo da suke masa suna sake maimaita kan su tare da bada fassara akan halin da ya riski matar sa a ciki , Hannun sa ya kai da ƙarfi ya jawo ta ya jefa kan ta kan ƙirjin sa yana jin yadda iskancin kukan da take yana sake dagula masa lissafi , Ɗan Allah ki min shiru   Yace da ita , a tsawace Da yake daman kukan gulma ne sai tayi luf kafin gajiyar biki tare da gajiyar farkon daren su danne ta bacci me matuƙar ƙarfi da daɗi ya silalo ya chafke ta , A hankali ya zame ta daga jikin sa ya miƙe daga kan gadon , rigar baccin sa ya ɗauka ya saka , ya fara taku yana barin ɗakin , Yayi zurfi a cikin tunanin abun da ka iya je ya dawo cikin rayuwar sa , mama ita take ta kai kawo cikin ran sa , rayuwar ɗiyar sa yake hangowa , yana jin wani irin al'amari me girma wanda yake tafe da tsoro akan ta , yana son tsare ta , so yake ya boye ta kar laifin da ya aikata ya shafe ta , tsoro yake kar tarihi ya maimaita kan sa , Bakin cikin da yake shaƙa kaɗai a wannan daren yayi masa yawa ma , me yafi ka san cewa matar ka tayi tarayya da wani ta hanyar zina sanya bakin ciki da ruɗani a cikin rai ?? Wani irin kishi me tsanani yake ji , wani irin yanayi yake ji akan ta , ji yake ƙimar ta na zubewa tana zagwanyewa daga ran sa tamkar narkakkiyar roba a cikin wuta , ji yake tamkar yana ƙyamar ta , ," yaya maimounatu zata min haka,"??     Yake tambayar kan sa , yana sake maimaitawa ,   Meyasa ? Meyasa ? Wai meyasa ? Bai san cewa ya fito har harabar gidan ba sai da ya ji ƙaƙƙarfar iskar dake wajen tana ɗaga rigar sa da bai ɗaure maɗaurin ba , a hankali ya kai hannu ya ja igiyar yana ɗaurewa , Tun da ya fito idanun ta suka sauƙa a kan sa saboda daman ta gagara bacci ban da juyi babu abunda take , ita mace ce me zafin kishin abunda take so , dan haka sanin cewa da tayi yau ɗin biyamurdi zai kasance da gimbiya maimouna ya ta'azzara soyuwar ran ta , ya sa bacci gagara ɗaukar ta duk kuwa da iya satar sa ,    Dan haka ta fito ta barandar ɗakin ta dake sama tana iya hango gaba ɗayan harabar gidan ta kurkusa daga inda take , duk kuwa da sanin da tayi dare ya raba ƙarfe 1:30am , to amma zafin kishi haɗi da bagen so ai rufe idanun me su suke yi .   Me ya fito da shi a wannan daren ??    Ta tambayi kan ta Ta san shi farin sani kamar yadda duk wani motsi nasa yake kusa da zuciyar ta , take kuma iya fassara kowanne motsi nasa Kada dai inda ya saba fita ya tafi a dai-dai wannan lokacin ya nufa ?? Wani irin tashin hankali ta ji ya taso mata ,    Zato take ya daina ? Tunda tun bayan dawowar sa daga nigeria bata ji alamun fitar sa ba , bata kuma gan shi ya fita ba , Tunanin ta ya katse lokacin da ta ga ya ɗaga kan sa sama tare da waiwayowa sashin da take ,    Da sauri ta tsugunna tana ɓuya a bayan ginin gaban barandar , Cigaba yayi da kallon sashin nata lokacin da zuciyar sa ke kitsa masa wataƙila ita ma wannan ɗin da aka liƙa masa , ta riga ta gama sayar da nata mutuncin a waje , ya dangana kome da ya faru a matsayin hakkin baiwar Allah yakaka da ya ɗauka , ya jagorance ta suka aikata mummunan laifi , shi daman Alhaki ai kuikuyo ne .! ***** Asubar fari ya hau shiri , garin baki ɗaya yayi masa wari , so yake ya tafi , yana son zuwa ya ga mama yasan ganin fuskar ta ne kaɗai zai iya sassauta masa zafin da ran sa ke yi , Daga sashin sa kai tsaye cikin gida ya tasamma sashin hajiya umma ba tare da ya dubi sashin kowaccen su ba tsakanin sashin gimbiya maimouna da tun barin sa da yayi cikin dare da sashin siyama wacce bai ko kai da sanin launin kayan da suke cibge a ciki ba , Yana ratsa sararik gidan yana amsa gaisuwar bayu da hadiman da suke kai kawo suna gyaran gidan da sanyin safiyar . A falo na ciki ya tadda hajiya umma tana Azkar , gefen ta ɗan ƙaramin tire ne da aka jera gorar ruwa da ƴan kofunan gilashi , Tana ganin sa farin ciki ya bayyana kan sa bisa fuskar ta , cikar haiba da mutuntukar da ta hango tare da shi ya sa ya yi mata ƙwarjini a yau , tabbas aure cikamakin addini ne , cikin sa akwai martaba tare da girma me yawa , Gaishe ta yayi sai dai saɓanin da da yake shigewa kusa da jikin ta , yau ɗin tanƙwashe kafafun sa yayi a gaba kaɗan da ita ya sunkuyar da kan sa , Kallon tsanaki tayi masa ba sai ya faɗa mata ba ta san yana tare da damuwa me girma wanda a jiya kafin rabuwar su da yamma babu wannan damuwar a tare da shi , dan haka take hasashen ko menene damuwar sa tana da alaƙa da iyalan sa , ita kuma bata da burin zama ɗaya daga cikin iyayen da suke bincikar rayuwar gidan auren ƴaƴan su dan haka sai ta yi kamar bata ga damuwar ta sa ba , ta matsa zuciyar ta da ke son sanin meye ya same shi ? Yaya kwanan ɗiya na su dukkanin su da fatan kun tashi lafiya ? Basu da buƙatar wani abu ? Duk kowa lafiya umma na basu buƙatar kome ,   Umma zan tafi bakin aiki doumin an ƙira ni daga niamey bisa ga wani aiki na gouggawa da ya taso , Aiki ? Ba an baka houtu ba na tsawon sati gouda ? Umma aikin mu na kare rayuka da dukiyoyin al'umma ne koyaushe ana iya ƙiran mu kuma a kowanne yanayi da lokaci , ! Shiru tayi tana nazarin sa , kafin ta jefo masa tambayar da ta sanya shi ɗago kai Tare da siyama zaku tafi kou ? Shiru yayi kafin ya tattaro ƙarfin halin da ya yi masa saura      Niamey zan tafi ba dosso ba Umma , idan na dawo daga niamey zamu tafi dosso tare. bata jaa ba tayi masa addu'o'i kamar yadda ta saba tare da ƴan nasihohi , ƙarshe ta sake tunasar da shi girman nawin da ke kan sa a yanzu , ! **** Tunda ya hau kujerar zaman sa a jirgin da zai ɗaga da shi zuwa niamey ya zurfafa cikin tunani daki-daki , Da hantsi ya samu isa ƙofar gidan , kan layin shiru , da yake unguwar babu yawan mutane , ya cire ƙuɗin me taxi ya biya shi , ƙarasawa yayi jikin ƙofar gidan ya ƙwanƙwasa Hajja wacce take tsakiyar sharar ƴar harabar gidan ta saurara da kyau ta tabbatar cewa gidan nasu ake bugu , ta ajiye tsintsiyar ta ƙaraso jikin ƙofar ta tambaya wanene ?? Hajja ni ne ,     Ta shaida muryar sa dan haka ta zare sakatar ƙofar ya samu shigowa gidan , sai fara'a take masa tana lale marhabin da shi ,    Shiga ciki Babban soja bari na ƙarasa ture ɗan wajen nan zan zo mu gaisa , sannu ka sha doguwar tafiye ince kwana kayi a hanya ? Murmushi yayi ba tare da ya amsa mata ba ya sanya kai cikin gidan , Ƙiiii    Ƙarar turo ƙofar sa ta sanya ta ɗago kan ta ta dubi sashin da ta ji motsi ,    Hajja sannu da aiki ! Tace cikin ƴar muryar ta , Bai amsa ba saboda baki ɗaya hankalin sa da idanun sa na ga fuskar mama wacce take jingine da jikin falmata akan cinyar ta  , su duk biyun suna fuskantar , Taku ya fara yi yana jin yadda shauƙin son ta ke ɗibar shi , da sassarfa ya ƙarasa gaban su ya tsugunna gami da kai hannun sa ya kama ƴan kafafun ta da suke sanye da ƴar safa ya sunkuyo da fuskar sa ya sumbata yana me rufe idanun sa da jin yadda ƙaunar ta ke sake ratsa shi tare da wata nutsuwa ta musamman , me yake ƙauna irin ta tsakanin ɗa da iyaye ƙarfi tare da tsafta ??. Lokacin da ya ɗago kan sa falmata ta kawo hannunwan ta duk biyu ta ɗora akan fuskar sa , a hankali tayi yawo da hannuwan ta tana shafar fuskar sa da idanun sa ke rufe , Tamkar wuta ta jaa ta ta janye hannuwan ta da sauri , tana ɗauke mama ta ɗora kan kafaɗar ta ,   Da farko tayi zaton hajja ce ta shigo, sanin cewa daga ita sai hajja a gidan . Wa-waye ne ? Tace tana ƙoƙarin miƙewa ,       Koma ki zauna Fatima ni ne , Ya kai hannu yana ƙoƙarin karɓar mama , Ta gane muryar sa dan haka ta sakar masa mama a hankali , tana dai-daita numfashin ta da firgici ya sa shi hargitsewa , Yana karɓar ta yayi mazauni akan ɗaya daga cikin kujerun wajen ba tare da ya janye idanun sa daga kan ta ba ya shiga sumbatar kumatu zuwa goshin ta , Bai ko ji gaisuwar da falmata wacce ta zauna daga ƙasa a gefe take yi masa ba ,     ita ma shiru tayi ganin bai amsa ba Shigowar hajja ya sanya shi rungume mama a jikin sa suna gaisawa shi da hajja ,      Soja garin nan na ku kuwa ya karɓe ka , ka ga yadda kayi fes da kai kana ƙyallin fuska sai ka ce sabon ango ? Ah lalle miyar umma da zaƙi ta sa kayi shar da kai duk wannan hautsinewar sojin sun kau , ke Fatima kin kuwa gaishe da maigidan naki ?? Na gaishe shi hajja , To ban ga kin kawo masa ruwa ba , ? Zata miƙe ya dakatar da ita ƙyale ta hajja ita da take da larura baza ta iya aike ba ! Ƴar dariya hajja tayi Zata iya Babban soja ai matar ta ka ba dama akwai lura da kaifin ƙwaƙwalwa saurin gane waje ne da ita , ka ga dai ba mu rufa wata guda ba a gidan nan amma ta haddace kusan muhallin kome da kome da yake cikin gidan nan , ita da kan ta take zuwa ta ɗau ruwa a firiza ko ta je kitchen ta haɗa madarar mama , kullum addu'a nake mata Allah shi kawo mata waraka . Ɗan murmushi yayi yana duban falmata wacce ta koma ta zauna ta juyar da kan ta gefe , Kalaman hajja sun tuno masa da abunda ya so mantawa , watau kai falmata asibiti tare da samar mata gurbin karatu , Ya zama dole yayi duk wani abunda zai iya yi gurin kyautata rayuwar falmata ko domin ya samu girman laifin sa ya ragu a wajen Allah . Hajja ku shirya zamou tafi babban hospitalisé a duba lafiyar idanun fatima yanzu. !    To to yanzu kuwa , falmata tashi ki shirya bari nima na ɗan kintsa , ! Niamey national hospitalisé nan suka je , inda basu wani ɗau dogon lokaci ba suka ga ƙwararren  ophthalmologist , bayan haske-hasken da tarin tambayoyin da yayi mata akan idanun nata , a ɗakin gwaje-gwaje . Suka dawo ofishin sa inda youssouf ke jiran su , bayani ya soma yi masa daki-daki A sakamakon binciken da nayi a zahiri ban hango wata cuta ba a idanun nata sai dai raunin ƙwayar idanun nata watau ainahin jijiyoyin idanun suna da rauni , a tambayoyin da nayi mata nayi ƙoƙarin sanin tayaya ta fara samun rashin gani ko da shi aka haife ta ?  amma sai ta shaida min bata da masaniya akan mafarin samuwar rashin gsnin ta , A takaice cikin binciken da muka gudanar da kuma sakamakon amsoshin da ta bayar yayin yi mata gwaji da akwai yiyuwar dawowar wani kaso daga cikin ganin ta idan har za'a samu ƙwararrun kayayyakin aikin da zasu taimaka wajen dawo da ganin nata , Sai dai a halin yanzu bamu da waɗannan kayayyakin a nan gida niger da sauran ƙasashe masu tasowa , sai a manyan ƙasashen duniya da suka yi fice wajen samun ingantattun asibitoci masu isasssun kayayyakin aiki tare da ƙwararrun likitoci , Dan haka a yanzu abunda zamu iya yi mata kaɗai shine zamu bata magungunan da zasu iya taimakawa wajen bada kariya ga idanun nata daga kamuwa da wasu cututtukan da zasu iya kassara sauran ƙarfin jijiyar idanun da kuma hana idanun yin ciwo ƙaiƙayi da zubar ruwa ,    Da fatan kun fahimce ni ? Mun fahimta Doctor mun goude zamu dawou gare ka idan buƙatar neman taimakou game da asibitin da ya kamata a kai ta a wata ƙasar ya tasou mun goude ƙwarai Madallah . Washegarin ranar Biyamuradi bai zauna ba , ya shiga binciken makarantar makafi me kyau da yake son ya kai falmata ta fara karatu kafin lokacin da zai sake yunƙuri me ƙarfi akan lafiyar idanun nata a karo na biyu . Association Nationale Pour la promotion des aveuglés , nan ne inda ya ji gamsuwar sa akan ya kai falmata nan ta fara ɗaukar darasi , wacce jibiya ce ta koyar da makafi tare da basu tallafi me tushe daga ƙasar amurka , da ta tanadi ƙwararrun malaman makafi , Cikin sati guda yayi mata rajista da duk wasu abubuwan da ya kamata , ya samar mata da direba bayan ya sa an kawo masa ɗaya daga cikin motocin sa da suke maradi ya danƙa makullin ga hajja wacce take cike da farin cikin wannan cigaba da falmata zata samu a rayuwa . Ranar da zai bar garin zuwa bakin aikin sa jahar dosso , ya yi musu sayayyar kayan abinci da abubuwan da zasu iya buƙata tare da ƴar ƙaramar waya me sauƙin amfani ya ba wa hajja bayan ya zuba mata lambobin sa a wayar ya adana ta su a ta shi wayar , Suna zaune a falo yana musu sallama akan yau zai koma bakin aikin sa , sai kuma zuwan ƙarshen wani watan zai komo Godiya me tarin yawa hajja ta yi masa ,     Ya amsa tare da waiwayawa sashin falmata da take ta faman lila mama akan ɗan lilon ta wanda baban ta ya sayo mata su tarkacen kayan wasan yara iri-iri har da wanda ya fi ƙarfin shekarun ta , tun daga kan lilon yara , kekunan koyon zama har zuwa ƴar mota ta yara da ƙananun kayan wasanni irin na ƴaƴan gata na sosai  , bayan suturun da ya daɗa jibgo mata.    Fatima baki da wata matsala kou ? Shiru tayi tana ɗan lila mama a hankali ,   Falmata hala kin samu kurunta ? Kina jin Babban soja na magana kin yi shiru ? Uhum yau ni naga abunda ya shallake tunani na ,      Babu kome kawai ina son unmh     Uhum ina jin ki me kike so ?? A kaini makaranta   Ai na sanya ki makaranta fatima sati me kamawa zaki fara zouwa ,! Na islamiya ? Ina so a cigaba da koya min karatun addini ma ,! Toh babu damouwa idan Allah ya yarda zan bincika a samu me koyar da ke na Islama ma , Akwai wata damouwa bayan wannan ? Daman ka gaya musu zan dunga zuwa da mama makarantar ko ? Babu inda zaki dunga goyon ta kina tafiya da ita anan waje na zaki dunga barin ta idan ya so kafin ki dawo na sauya ta , ko kuwa na gudu da ita,  kina nufin baza ki maida hankali kan karatun naki bane ? Zaki dunga ɗaukar ta kina zuwa da ita makaranta ki ɓige da raino memakon karatu ni ke meyasa ana nuna miki hanya kina daɗa bauɗewa ne ?? Ɓata rai tayi ta ɗauke kai Murmushi youssouf yayi , shi dai rigimar hajja da falmata na ba shi dariya  Duba fatima ki bar mama a wajen hajja har ki tai école ki dawo Kin ji kou ?  Ba'a tafiya da yara école. Shiru tayi idanun ta na kawo ƙwalla ita dai bata ƙaunar abunda zai raba ta da mama ko na ƴan mintoci ne bare fa makaranta da awanni zata yi a can , kai anya zata iya , ? To hajja mu dunga zuwa tare da ke mana makarantar ? Sai ki dunga riƙe min mama nayi karatun na fito ? Ke raba ni da wannan gudun birin , gotai gotai da ni zani makarantar ? Yaushe rabon duniya da ayyaraye ?  Babu inda za ni ke kaɗai zaki tafi makarantar ki ki dawo ki same ni ina nan , ilmin ai shine Babban gatan ki falmata kin ji ko ? Naji hajja Yauwa mutuniyar ai shiyasa nake son ki akwai ki da saurin fahimta , Sallama suka yi da youssouf yana sake yiwa hajja godiya me tarin yawa tare da ɗanka mata ƴan kuɗaɗe wanda da kyar hajjan ta yadda ta karɓa sai da yayi ta roƙon ta da Allah  . Daga nan Dosso yayiwa tsinke bai jin marmarin zuwa maraɗi duk da cewa fiye da kaso talatin na ɓacin ran sa game da sha'anin sa da gimbiya maimouna ya kau , domin har sun yi waya ma cikin kwanaki biyun .    Assalamu Alaikum kowa da kowa ! Da fatan kuna lafiya ? Ina neman afuwar ku bisa jinkirin zuwan wannan shafin , hakan ya faru ne sakamakon tafiya da ni zuwa gida , ban samu zama ba ziyarar dangi da sauran Al'amuran yau da kullum . Da fatan zaku cigaba da haƙuri da tsaikon da ake samu cikin ajizanci irin na ɗan Adam ? Nagode     [9/3, 10:14 PM] +234 806 122 1116: Fikrah writers association MAFARI ( Hargitsin Rayuwa ) Umm'muaz 32 Bayan Shekaru Biyar Lokaci baya jira sai dai a jira shi , ba'a masa shamaƙi a yayin wucewar sa , Lokaci gudu ne da shi fiye da saurin  bugun zuciyar ɗan adam , Lokaci yayi juyi ya juya ya zo da sauyi ta mabanbantan fuskoki a rayuwar mutane a cikin tsawon shakaru biyar . Yakaka tana ɗaya daga cikin mutanen da suka samu sauyi ta fuska me kyau tare da tarin nasarori daki-daki cikin rayuwar ta , wanda a yau ta kawo matakin kammala makarantar ta secondry wacce ta rayu tsawon shekaru biyar tana faɗi tashin neman ilmi a cikin ta , da jajircewar ta tare da nuna ƙwazo ya sa aka ɗaga ta aka mata tsallaken aji na shekara guda daga jss3 zuwa ss2. Da hakan ya kawo kammaluwar karatun nata cikin shekaru biyar kachal . Ta fito da sakamako mafi kyau da ya sanyata farin ciki ita da duk wasu makusantan ta musamma malama maryam da lubna waɗanda da jajircewar su cikin taimakon yakaka a harkar ilmin ta har ta kawo wannan matsayin . Samy baby ma wacce ta tashi daga matsayin samy baby ta koma ,Hajiya samira ,"  ita ma ta taya yakaka farin cikin kammala karatun ta wanda duk wasu kuɗaɗen hidindimun karatun daga farkon sa har ƙarshen sa ya fito ne daga aljihun Alhaji Gali da har kawo yau suke liƙe a naniƙe da juna , bata da wata maraba da matar sa , kai har ma ta zarta matar sa ta aure iko da shi tare da samun kuɗaɗen hannun sa , Alhalin kuwa har yau da suke samun wajen shekaru takwas tare sun gaza yin aure ."illar bariki kenan ,! Karo na uku yakaka ta ajiye ƴar madaidaiciyar taɓaryar hannun ta da take dakan fura da ita , ta murza tafin hannun ta da suka yi ruwan hoda hoda saboda dakan da basu saba yin irin sa ba ,    Ta ɗago fuskar ta tana yamutsa ta , Ummi wallahi nagaji da dakan nan ɗan Allah ummi a min sassauci ki yadda na tafi ko'ina ne cikin garin nan na nemo furar nan nayi sadakar nan da ita , Allah bazan iya yin fura da hannu na ba , Malama maryam wacce take zaune daga gefe akan kujerar tsakar gida tana karatun littafin Al'mauduat Al'kubra , ta ɗan janye littafin daga fuskar ta    Fuskar ta babu alamun wasa ta ce ,    Sai fa kin daka furar nan yakaka kiyi sadaka da abunda kika sha wahala wajen samun sa yafi ɗaukaka darajar sadakar ki a wajen ubangiji , tsawon shekaru biyar kina faɗi tashin neman ilmin nan , a yanzu kin samu kin kai wata gaɓa me kauri ashe baza ki iya dakan fura kaɗai kiyi sadaka domin nuna godiya ga ubangijin ki ba ?? Jikin yakaka a sanyaye ta amsa    Zan iya ummi , To maza kiyi sauri ki gama dan shabiyu ta kusa , kar har  a sauƙo daga juma'ah baki gama ba kin ga kamata yayi a ce ki rabar da ita ga mabaratan da suke bakin masallacin juma'ar unguwar nan kin ji ko ?   To ummi tace tana saɓar taɓaryar ta fara daka ,    Lubna wacce take zaune a gefe kusa da ita kan ƴar darduma tana yankar ƙumba , ta ɗago kan ta fuskar ta da murmushi ta sanya hannu cikin faffaɗan kwanon silver da aka ajiye guntun dafaffiyar furar da ba'a kai ga daka ta ba , ta gutsuro wata ƙatuwa ta sake jefawa cikin turmin da yakaka ke daka ,    Yauwa ƴar ummi yi maza ki daka,  na ɗebo madara na fara damu ni ce ta farkon sanya Albarka a result ɗin nan kin sani ko ?    Ummi kina ganin ta fa ? Tana ƙara min wata bayan na kusa gama dakan   Lubna maza ajiye nails clipper nan ki karɓi dakan nan ki taya ta ,    Ta furta hakan tana gyara zama gilashin idanun tana cigaba da karatun ta .   Ummiii , dan Allah ni lokacin da nayi nawa dakan futar gama makarantar ta taya ni Haba ummi dan Allah,    Wallahi na taya ki kin manta ranar ....    Yanzu aikin samun ladan kuke yiwa haka ?    To shikenan duk ku bari ni zan zo na ƙarba nayi tunda da alamu ku lada yayi muku yawan da ya sa har kuka fara gudun sa ,   Da sauri lubna ta zaburo tana ƙoƙarin karɓe taɓaryar hannun yakaka ita kuma yakakar ta riƙe gam ta hana ta ,   Dan Allah ki bar ni na taya ki kin ji sahiba ta.     Tare da marairaice murya   Naƙi ɗin  , nima zan daka kaya na duk na mulmula na ɗau abuna a kai naje na rabar , kin ji sahiba ta . Wayar lubna da ta ɗau kiɗa ita ta raba musu gardama    Cikin sauri lubna ta ɗau wayar ta ta yi hanyar falo tana satar kallon ummi wacce bata nuna alamun ta san duk abunda suke a wajen ,   Yakaka ta bi bayan ta da kallo tana murmushi Ta kai gaf da shiga falon ta ɗaga murya tana cewa ,    A gaishe min da yayan namu da kyau da kyau kin ji sahiba ta ? Da gudu lubna ta ƙarasa shigewa falon tana dariyar jin kunyar ummi . Ƙarfe biyu dai-dai da idar da sallar juma'a yakaka da lubna sun kammala ɗaura fura guda uku uku a cikin farar leda tare da kindirmo me ɗan dama shima a ƙulle a leda daban , suka haɗa su suka zuba a ƴar bakar leda daban daban , ba laifi dayawa , Yakaka ta jaa hijabinta saka lokacin da ta gama saka socks ɗin ta a kafa ta zura hijabin tana kallon lubna wacce take ƙoƙarin ɗaura niƙaf ɗin ta ,    Sahiba dan Allah muyi sauri kar mabuƙata su watse ,     Taku biyu tayi ta ɗauko niƙab ɗin ta ruwan madara , mahaɗin hijabin ta ta  fara ƙoƙarin ɗaurawa a fuskar ta , Da sauri lubna ta riƙe niƙaf ɗin ,   Haba sahiba ta ? Ina mun yi cewa kin daina saka niƙab ɗin nan haka sai bayan kin yi aure ?? Hararar ta tayi    Shiyasa na ga ai kema yanzu da za ki fita babu naƙib ɗin a fuskar ki , ni dan Allah sakar min mahaɗin kwalliya ta , cikamakon martaba ta ,na sanya abuna ,    Amma ai ni kin san dai an riga an sanya rana , babu sauran wani ɗa namiji da zai sake cewa yana so na na kula shi ,    Ok to maza yi min gorin aure sahiba ,    Ta furta hakan muryar ta babu alamun wasa .   A hankali ta sakar mata niƙab ɗin , Allah ya baki haƙuri sahiba ba manufata ba kenan .  Mu tafi . Yakaka wacce bata furta zancen da wata manufa ta daban ba daga cikin ran ta sai domin ta samu lubna ta sakar mata niƙab ɗin ta da take neman ƙarfi da yaji ta hana ta sawa a cewar ta shi yake hana samari kula yakakar tunda ba ganin fuskar ta suke ba , duk sai ta ji ta ba daɗi da ta ga kamar zancen ta ya sa aminiyar ta a damuwa . Tafe suke akan hanyar su ta dawowa daga rabar da furar suna tafe suna hirar su hankali kwance irin ta shaƙiƙan ƙawayen da halin su da ra'ayoyin su suka zo ɗaya suke kuma ƙaunar juna domin Allah , Motar da take tahowa daga bayan su sannu a hankali saboda ruwan sama  da ya kwanta bisa kan kwaltar , wacce ta fito daga layin gidan su yakaka ,ita ce ta matsa musu hon , Su biyun suka haɗa ido , yakaka ta janye hannun lubna , da nufin ko Suna bisa hanya ne sun matsa daga hanyar , Maza biyu ne a cikin motar wanda kallo guda za'a musu a gane cewa ba ƙananun samari bane , mazaje ne waɗanda suke kan ganiyar shekarun su na 40 cif , wayewa tare da gogewar da ta bayyana kan ta a jikin su ita take nuni da tarin ilmin da yake jibge a ƙwanyar su , ɗaya yana mazaunin direba yayin da ɗayan yake daga gefen sa , Na gefen ya kai hannu a karo na biyu da nufin sake danna hon , na gefen nasa ya tare hannun nasa ,   Suleiman meye hakan kake kuma ? Yace yana kai kallon sa gare shi ,    Dan Allah abokina yi parking ka bani mintuna biyu zan fita ,   Bai ce masa ƙala ba saboda yanayin sa da bai tare da nishaɗi ya sa baya buƙatar doguwar magana , ya gangara daga gefe ya tsayar da motar , Da sauri suleiman ya fice daga motar , A hankali yayi musu sallama cikin nutsuwar da take halittar sa tun ƙuruciya , Tana jin muryar sa ta gane shi , shine dai maƙalemata manne matan da ya liƙe mata tsawon shekaru uku yana bibiyar ta ba tare da ta taɓa saurarar sa ba , Matsa hannun lubna da yake cikin nata tayi , ta mata alama da kar ta kula sa , sai dai irin nutsuwa tare da kamala da ƙwarjini na musamman da lubna ta hango a gare shi ya sa ta fahimci ba irin sa ne mazan da mata ke gwatsalewa ba dan haka taƙi amfani da umarnin yakaka ta ja ta tsaya tare da amsa sallamar sa  Baiwar Allah naji daɗi da ki ka tsaya kika amsa sallama ta domin nasan da ta ƙawar ki ce baza ku tsaya ba , dan kuwa tsawon shekaru kusan uku kenan ina bibiyar ta amma bata taɓa tsayawa ta saurare ni ba,   Da sauri lubna ta kai kallon ta ga yakaka wacce ta yi gaba kaɗan ta tsaya tare da ɗauke kai daga barin kallon su . Dan Allah kayi hakuri, tace da shi , girman sa na sake cika mata idanu Babu kome duba da cewa a yanzu bisa titi muke ba darajar mu bace yin magana anan dan haka ki sanar da ni adireshin da zan same ki ko kuma number ta wayar ki saboda ina son yin magana da ke game da ƙawar ki idan kin bani dama , Da sauri lubna ta ba shi number wayar ta , tana jin farin ciki na ratsa ta , a karon farko yau wani namiji ya nuna yana da ra'ayi akan yakaka , namijin ma gangariya irin wannan ai kuwa yau ummi na da farin labari . Bayan ya karɓi number yayi mata sallama ya juya wajen motar su , da ƴar dariya a fuskar sa ya dubi abokin sa da hankalin sa ke gefe guda da alama yayi zurfi cikin tunani . Abokina ka taya ni murna ga alamu na sanya ƙafa a kasancewa mijin mata biyu , ramla ta kusan samun abokiyar zama , tsawon shekara uku da nake bin yarinyar nan tana yin biris da ni , sai yau nayi sa'ar haɗuwa da ƙawar ta ga alamu ita zata min tsani na samun ta ,  na rasa me yake fusgata akan ta alhalin sau biyu kawai na taɓa ganin fuskar ta , Da alama akwai rabo ne a tsakanin mu me ƙarfi , A hankali ya tada motar ba tare da ya bada muhimmanci a zancen nasa ba , To ai sai ka ɗau harama , takaicin matan duniya ne bai ishe ka ba , ko kuwa ma nace har yau baka san wacece mace ba da irin tarin abubuwan ƙi da yake tare da ita da ace ka sani da baza ka yi sha'awar ajiye su har su biyu kamar kayan ado a gidan ka ba , Wuce su suka yi a hankali , Lokacin da suleiman ke bashi amsa Hamza kenan kai dai na rasa wanne irin tabo mace tayi maka a duniya kake musu irin wannan kuɗin goro , duk kuwa da yadda safiyya take tarairayar ka tare da lelen ka kamar wani jariri sabon haihuwa , bana jin ta taɓa saɓa maka a rayuwar zaman auren ku . Ya ƙarasa zancen tare da dariyar shaƙiyanci . Murmushin takaici doctor hamza yayi ,    Baza ka taɓa ganewa ba suleiman ! Ya maida ganin ga madubin  motar sa , yana hango ta ta jikin madubin ƙwarai tafiyar ta ta ɗau hankalin sa , mace ɗaya ya taɓa gani da salon takun nan , wacce bai ko son giftawar tunanin ta cikin ran sa sai fa yau da ya sake ganin wata wacce fuskar ta take a rufe  Bai kai ga ganin kamannin ta ba . Yakaka ashe daman irin zaman da kike da ni kenan ??   Cewar lubna idanun ta na bayyana ɓacin rai , A kaikaice yakaka ta dube ta , kin ga sahiba bana ciki da rigima , daga kawai mutum ...   Hmm   Lubna ta katse ta , Wallahi sahiba abu ɗaya zan faɗa miki a matsayin ki na wacce na ɗauka ƴar uwa , Kar ki yadda kiyi wasa da damar da ta zo miki , idan har wannan mutumin da gaske yake ki bashi dama ku fahimci juna , aka yi bincike bashi da wani aibu wallahi ki bada dama kuyi auren ku shekarun mu sun fara tafiya ishirin da biyu mun rufa ta da uku muke hari ,wallahi wasa ba namu bane dama kuma sau ɗaya take zuwa a rayuwa ,   Shiru yakaka tayi Kalmar ,"Dama," na maimaituwa a cikin kan ta , ita har tana da wata dama da ta rage mata kuwa ? Ai damar guda ɗaya da take da ita ta riga ta zo ta wuce tun a shekarun baya , " damar da mahaluki ɗaya ya bata wanda ta tabbatar baza ta taɓa samun  makamancin sa ba, bata yi amfani da damar ba a maimakon haka ma sai tayi masa mummunan sakamo da har yau idan ta tuno shi kunya tare da nadama basa ƙasa a guiwa wajen danne ta , ina ma ina ma ina ma ?? Da ace dama zata dawo mata ? Da ace zai sake ba ta dama ko da gutsire daga irin damar da ya bata a baya ? Wataƙila da ta gyara kuskuren ta ta wata fuskar , , abunda ta sani shi ɗin ya riga ya mata nisa ita ta zama wata shuɗaɗɗɗan lamari da ya taɓa giftawa cikin rayuwar sa , Bata da wani shauƙi ko tunani mai armashi akan wani ɗa namiji har yau ta gaza sake son wani ɗa namiji , " zata iya cewa ta ƙi maza ," ƙi irin na wanda kunama ta taɓa harbin sa babu shakka idan ya ga gizo-gizo kakkaɓe shi yake , dangantakar nesa nesa ce ke tsakanin ta da maza , shiyasa har yau ta gaza samun saurayi ɗaya tak , ita ce bata saurarar su bata bada fuska , take boye kan ta tare da killace surar ta daidai da fuskar ta a rufe take , ta zaɓi hakan , ta kuma fi son tayi tsarayuwar ta a haka ba tare da wani ɗa namiji ya sake ratsa rayuwar ta , burin ta ɗaya ne shine tayi ilmi kuma tana godiya ga Allah tana godewa malama maryam tare da addu'ar Allah saka da alkhairi ga baki ɗayan zuri'ar ta , Ko da ko kusa bata sahun malumma amma kai tsaye a yau ta wuce a ƙira ta da jahila , ta nemi ilmi tana kan nema kuma zata cigaba da nema har.....    Har suka kawo gida bata cewa lubna ƙala ba ,    Sai da suka shigo gidan ta ruga da ɗan gudun ta ta rungume malama maryam wacce take tsaye daga ƙofar kitchen tana amsa sallamar su .   Ni bazan yi aure ba har sai nayi ilmi na zama kamar ummi malama ta , sai ki san yadda zaki yi da mutumin da kika ba wa phone number . Murmushi ummi tayi ,    Anya kuwa yakaka ? Aure ai shine cikar darajar ɗiya mace Lubna wacce take zama akan kujera ta shiga bada labari tiryan tiryan tana yi tana hararar yakaka wacce take yanka musu cabbage da zasu ci abincin rana da shi . Sosai malama maryam ta yiwa yakaka faɗa daga ƙarshe ta ƙarƙare da yi mata nasiha tare da faɗa mata fa'idojin aure da girman matsayin sa a addini . Jikin yakaka yayi sanyi har idanun ta na tara ƙwalla , ta gaza cin abinci na kirki . A ƙarshe ta jaa kunnen ta akan daga yau kar ta ƙara ƙin saurarar duk wani namijin da yake da kamala da ya nuna yana son ta , ta ƙoƙarta ta saurare shi na ɗan wani lokaci ta fahimci wanene shi , daga nan idan ta yarda da halayen sa na ƙwarai ta bashi dama ita ma tayi aure , ko kusa kar ta kawo aƙidar ƙin aure kusa da ran ta saboda wani shuɗaɗɗan dalili nata , . A ladabce ta amsa mata da zata yi yadda ta faɗa mata . Bata wani jima ba saboda yadda walwalar ta tayi ƙaura ta musu sallama tana barin gidan ƙarƙashin rakiyar lubna wacce duk ta damu da rashin walwalar ƙawar ta ta , sai faman jan ta da hirar raha take , Har ƙofar gida ta rako ta , Zata tura ƙofar gidan ta shige lubna ta riƙo hannun ta , ta waiwayo tana kallon ta da sakakkiyar fuska . Sahiba idan baƙya son sa idan ya ƙira insha Allah zan faɗa masa dan Allah ki bar damuwa . Murmushi yakaka tayi ,    Ni dai ban ce miki ba , kawai ....shiru tayi ,     Baza ki gane ba sahiba . Zan gane dan Allah ki faɗa min meye ne ? Duk banji daɗi ba da naga ranki a jagule Ni bana son kowanne ɗa namiji ilmi me zurfi nake da burin yi saboda ina da mummunan rauni a zuciyata wanda jahilci ne ya assasa min ina so na samu ilmin da zai warkar min da ciwon da na ji akan jahilci , A hankali lubna ta gyaɗa kai tana sakin hannun ta ,   na fahimta, ta furta hakan ba domin ta fahimce ta da gasken ba , abunda ta daɗe da sani cewa yakaka tana da wani binannen ƙuduri wanda take dakon sa boye cikin ran ta da ita bata riga ta san wanne irin kuɗiri ne ba . Daga cikin niƙab ta sake yin murmushi ,    Sahiba sai gobe zan zo ki bani labarin yadda kuka yi da ,"direba,"    Ta ƙarasa zancen da dariya cikin muryar ta , ko kafin lubna ta bata amsa wacce ta yamutsa fuska tare da ƙanƙance ido   Ta shige gidan da ɗan gudun ta tana jin lokacin da lubna ke cewa daɗin abun ma direban jirgin sama ne . Da sallama ta shiga falon duk da cewa tayi ne ba domin tana sanya ran za'a amsa mata ba sai dan sanin muhimmancin sallama a musulunci da ta riga tayi . Kamar yadda ta zata kuwa daga samira har hamshaƙiyar ƙawar ta da take haƙimce akan kujerar falon babu wanda ya amsa sallamar ta , hirar su suke cigaba da yi da take cike da shewa da dararraki irin na yaran matan da suke juya duniya a tafin hannun su . Rage tsawo tayi ta ɗan durƙusa , Anty samy sannu da hutawa , Ke ke yaks wanne irin iskanci ne wannan ?? So nawa zan faɗa miki bana son kina shigo min gida da wannan maya-mayan yadikan da kike yawo da su a jiki , musamman ma na fuskar nan taki kamar wata korarriya daga makka ? To na faɗa miki yau ce rana ta ƙarshe . A hankali yakaka ta kai hannu ta kunce niƙab ɗin fuskar ta , lokacin da sofi take kai ganin ta kan ta , Kiyi hakuri anty na cire . To ya dai fi miki , yo Allah na tuba na sanya wannan mayanin a fuskata ai ya shaƙe min numfashi ya sheƙa da ni barzahu ban shirya ba , Kallon kallo suka yi a tsakanin su , kafin sofi ta janye idanun ta tana yatsina fuskar da ya zama halittar ta , Kirjin yakaka yayi dakan lugude , tsawon shekaru biyar bai isa a ce ta manta fuskar sofi ba matar da ganin farko haɗuwar su ta fari ta ɗau karan tsana ta aza musu ita da ƙanwar ta falmata , dan haka cikin hanzari ta miƙe tare da haɗiye kalaman gaisuwar da tayi niyyar miƙa mata , ta juya tana nufar ɗakin ta  . Friend wannan wacece ? Aina kika samo ƴar ƙwara ? Ko dai ko dai .... Ta ƙarasa zancen tana sakin wata shashashar dariya . Ɗan murmushi samy baby tayi cikin ran ta bata mamakin rashin gane yakaka da sofi ta yi , ko ita da kan ta bata gajiya da kallon yakaka , wata irin fata ce da ita wacce bayan haske tana ɗauke da wani irin taushi tare da ƙyalli a idanu , ya haɗu da gyara tare da jimaka me kyau da take samu daga ita samy baby , haɗi da girma tare da cikar macen da take kan ganiyar ƙuruciyar ta , sai ta zama tamkar farin wata idan ta gifta dole ta ɗau hankali , ɗan tsararren jikin ta da yake a murmure kowanne irin kaya ta sanya masa kyau yake . Ai ba domin tirjiya da yakakar take gwada mata ba da tuni maƙudan kuɗaɗe sun fara shigo mata ta hanyar yaks , amma wani ɗan lokaci kaɗan take jira wanda zata kammala aiwatar da nufin ta , ta kuma fara kwasar adashen da ta dunga zubawa a dalilin ta ,   Friend wannan wata haja ce da nayi tsintuwar ta a gari  ,     Kalaman samy baby suka zo daidai da zaman yakaka a bakin ɗan gadon ta , daga inda take tana iya jin muryoyin su ,    Daɗi ta ji da samy baby bata jaa dogon bayani ta sanar da sofi ko ita ɗin wacece ba . Taɓ kina nufin wanna ƙatotuwar budurwar kika bawa mafaka a gidan ki ? Ah lalle ,   ta ƙuta      Kawai dai dan ke ma ba miji ke gare ki ba , idan ba haka ba ina ke ina kawo annoba muhallin ki ?    Ai ni tsakanina da ire-iren waɗannan matan masu kama da barbarar yanyawa ko gaisuwar kan titi babu ,     Ai ko sama da ƙasa zasu haɗu bazan bar ido irin na yarinyar nan ya gauraya da na doctor na ba ,     Wai Allah har bugun numfashi na ya fara sassarfa bala'i .   Dariya samy baby ta kwashe da shi , daɗi na da ke freind akwai bala'in kishi ,     Sha kurumin ki sanya ranki a sassanyar inuwa tunda har kika mallaki doctor hamza a matsayin miji ke da kan ki kin san naki ne ke kaɗai mutuniyar ,     Wata sakaryar dariya sofi ta sake tare da ba wa samy hannun suka tafa . Ni yanzu kin ƙi ki faɗa min sirrin friend wai tsakani da Allah wacce duniyar kika samu haka a Boston da har kika ajiye waɗannan manyan kayan haka ? Kin gan ki kuwa sofi cikin shekaru huɗu jal kin sauya ta jiki , ai wallahi wanda duk  ya san ki a da da kike bulugari bazai gane ki ba a yanzu da kika koma wata katafila, ke ni anya kuwa doctor yana iya yin nisa da ke wannan irin abebaɗan more rayuwa da kika haɗa a jiki ahayye duniya gidan daɗi ɗan Allah ƙawata bani sirrin !    Kalaman samy baby na kusa da ƙarshe ya sa fara'ar fuskar sofi raguwa , Cikin jimami tace ,    Ai lamarin doctor ajiye shi gefe guda friend , kullum jiya iya yau ke wataran ma jiya ta fi yau ɗin domin ko yanzu kafin su kawo ni nan su ajiye baki ga yadda ya nemi min cin fuska a gaban abokin sa ba , akan sutura , wai kayan da na sa sun matse ni , bazan hau masa mota a haka ba sai dai na tafi na hau taxi shi babu abunda ya dame shi , ya dunga balbalin bala'i da daman ƙiris yake jira tun kafin mu baro US yake kumburi shi ɗaya uwa fulawar da yis yayi mata yawa,  ina dai lallaɓa sa ne , Wallahi tsawon shekaru uku da muka yi a US da zan lissafa miki irin baƙin cikin bawan Allah nan da na ƙunsa sai kin ji tausayi na , gangar jikin sa kaɗai na mallaka , ruhin sa na wani waje wanda nake zaton ya min nisa duk kuwa  ƙoƙarina akan kome nasa , ke dai kin san yadda daman aka yi auren nan namu , to duk da haka ban zauna ba malamai da bokayen yi nake na ƙarƙare miki ƙanƙat ɗin tsafi dai har india na je akan a min yadda zan yi na samu mazauni na dindin a gurin sa na amshi sararin zuciyar sa, Zuwa na karnataka india ne ma fa da aka min wani mugumugun aiki aka min filla filla da tunanin sa na samu yake kula ni har muke iya haɗa shimfiɗa , A hakan ban zauna ba kullum ni ce a gyara saƙo da lungu na jikina tare da matso kyau , rana ɗaya na lura kamar Yana son mace me manyan kaya , saboda bin wata mata da kallo da na ga yana ta yi a gidan cin abinci a boston , na dubi matar na ga idan banda himilin cinya da ɗuwawu bata fi ni kome ba , tun daga ranar na shiga faɗi ta shi ganin yadda zan yi nima na ajiye manyan kayan nan , magungunan ɗago ɗuwaiwai da ƙara faɗin cinya babu irin wanda ban afa ba , amma da yake jikin nan nawa marke ne , shiru maƙatau bulunbuƙui , jiya iya yau , na kasa haƙuri na faɗa miki tare da jagorar wata ƴar * ƙawa da nayi a boston balarabiya ce ƴar duniya ta ƙarshen ƙarshe  , ita ta kai ni aka min aiki me ƙanƙat , aka tatso tare da ɗago tudun bayan nan da kike gani , azaba babu irin wacce ban sha ba a lokacin aikin nan da bayan gama yin sa , amma na shanye , kuma babu shakka ƙwalliya ta biya kuɗin sabulu , domin wasu cin kashin da yake min da yawan fushin sun ragu , duk da dai da farko ya tada ɓallin sai na faɗa masa me naje nayi jikina ya koma haka ya dunga bincikata , da yake lokacin aikin nan na karnataka na kan zafin sa , zancen bai yi nisa ba ya manta ya kuma haɗu da shima yana son manyan kayan ai hajiyata shiru kike ji malam ya haɗiyi shirwa !    Sai dai ki ga idan na gifta yana zaune yana haka da ido ,"ta wani yi ƙasa-ƙasa da ido tana kwatance , " yana bin abebaɗan da kallo , ni kuwa sai na sake jujjuya masa su da kyau yadda zan sake kamo sa , a raina ina "faɗin kai da abubuwan ka ai daman sakin jiki kayi ka ƙure musu kallo meye na wahalar satan kallo kamar ba naka ba " ah to abun duniya menene ?? Sarkin fawa da kyautar ƙaho !     Wata ƙatuwar dariya me ɗauke da haniniya samy baby ta kwasa sofi tana taya , suka chafke   Shegiya tawan baki da kyau ! Watau shi tsuntsu me wayo ta wuya ake danƙar sa ,     Charaf kuwa     Ah to ai na faɗa miki friend babu abunda bazan yi ba babu kuma inda bazan shiga ba akan soyayyar doctor buri na ɗaya , shine ya kasance nawa ni ɗaya har abada ..    Kin kuwa kamo hanyar , ko ma nace kin isa ga matakin .!    Wata dariyar suka sake saki kamar sabbin mahauk.... Yakaka wacce dararrakin su ya mugun takurawa , saboda rabo da tayi da jin hayaniya sosai ya haka da kuma kalmomin su da basu mata daɗin saurare ta sanya ƴan yatsun ta biyu ta toshe kunnuwan ta , hakan bai mata ba sai ta ɗauko ƴar ƙaramar wayar ta wacce samy baby ce ta saya mata tana da memory a ciki wanda yake ɗauke da ƙira'o'in Alqur'ani izifi sittin tare da wa'azizzikan manyan malamai ta jawo ear plugs ta maƙala a kunnuwan ta , ta sanya ƙira'ar AlQur'ani ta fara saurara bayan ta jingina da jikin gadon nata . Niamey A ɗakin zaman marasa lafiya na musamman dake cikin national hospitalisé , mata biyu ne bisa kan ɗan gadon marasa lafiya , babbar ta jinginu da jikin sa ƙarfen gadon yayin da ƴar ƙaramar take kwance a jikin ta kan ta na bisa ƙirjin babbar dukkanin su biyu idanun su a rufe suke , Ɗan motsawa ƙaramar tayi tana yamutsa ƴar fuskar ta da take fayau ! Kafin ƴan daƙiƙai babbar ta buɗe nata idanun tare da tallafo ƙaramar ta miƙe zaune da ita sosai daga kishingiɗar da tayi ,     Sannu Mama , ya kike ji yanzu jiki ya daina ciwo ?     Duban fuskar maman ta tayi da raunanan idanun ta , ta kai ƴan hannuwan ta duk biyu ta ɗaura bisa fuskar mamar ta shafa tun daga goshin ta zuwa haɓar ta ,kafin cikin ƴar muryar ta me zaƙi irin ta yara masu wayo tace          Na ji sauƙi maama kin ji ko ? Da ɗan raunannan murmushi a fusksr falmata ita ma ta sanya hannu ta shafi fuskar mama yadda tayi mata ,    Naji daɗi mama na ta ji sauƙi ,Allah ya ƙara miki rangwame tare da sassauci , me zaki ci kafin ki sha magungunam ki ? ,    Mayar da kan ta tayi ta kwantar bisa ƙirjin mamar ta ,      Maama bana cin kome , ! Idanun falmata suka kawo ruwa tana jin wani irin ciwo daga ƙasan ran ta , ƙaƙƙarfan tausayin mama kamar kullum yana sake cin ran ta , da ace tana da dama da tayi musanyan jinin jikin ta da na mama wanda ke gauraye da ƙwayoyin ciwon da a kullum yake barazana ga rayuwar ta tare da sanya ta a tsananin ciwo , to sai dai bata da dama ciwon mama muƙaddari ne daga Allah tun lokacin samuwar halittar ta . Bai tare da cikakkiyar nutsuwa ya turo ƙofar bakin sa ɗauke da sallama , jin muryar sa ya sanya mama ɗagowa daga jikin falmata , ta waigo shi da buɗaɗɗun haƙoran ta ,   Papa !   Da sassarfa ya ƙaraso , ciɗak ya ɗaga ta tare da rungume ta tsama cikin jikin sa yana shafar lallausar sumar ƙan ta da take a tsefa an tufke mata ita a ƙeya . A hankali yayi baya yana zama kan kujera ɗakin ya tare da ajiye ta kan ƙafafun sa ya riƙo fuskar ta da hannayen sa biyu idanun sa na bayyana tsantsar damuwa da soyayya yace mata .    désolé ma chérie comment tu te sens maintenant ? ( sannu my dear ? Me kike ji yanzu?  Je me sens mieux maintenant papa!  ( naji sauƙi yanzu papa )     Ta furta hakan tana me shigar da kan ta zuwa ƙirjin sa ta kwantar da alamun rashin ƙarfi a tare da ita ,   Runtse idanun sa yayi da ƙarfi yana jin yanayin da ya gan ta a ciki na narkar da ruhin sa ,   A hankali ya ɗago kan sa yana duban sashin falmata daidai lokacin da ta kai ƴan yatsun ta tana ɗauke hawayen da ya biyo kan kumatun ta ,           Tausayin ta me ƙarfi ya taso masa ,      Fatimah , Ya ƙira sunan ta a ƙasan maƙoshi   Sashin da take jin tashin muryar sa ta waiga ba tare da ta amsa ba .   Meyyasa ba'a sanar da ni tashin ciwon mama ba ? Sai doctor ta ne daga nan ya ƙira ni yake sanar min ? Muryata ƙasa-ƙasa ta ce     Hajja ce ta hana a faɗa ma tace duk shekaranjiya ka tafi daga niamey , !      Miƙewa yayi tare da ƴar sa a kafaɗa bai ce kome ba , sai da ya kai bakin ƙofa yace mata     Bari mu tai ga likitan ta !      Bai jira amsar ta ba ya fice daga ɗakin .    Kichiɓus suka yi da hajja wacce take kan hanyar dawowa ɗakin bayan ta ɗan zaga ta motsa ƙafafun ta. Riƙe baki tayi nuna alamun mamaki ! O Ni , yanzu ashe Babban soja sai da ka taho ? Kai da shekaranjiya jiyan nan ka tafi bakin aiki ? Banda abunka ai mun riga mun saba mun kuma fahimci kan ciwon mama tana fara nuna alamun rashin lafiya da hanzari muke zowa da ita asibiti , ai da kayi zaman ka bakin aiki . Gaishe ta yayi a ladabce    ta amsa da sakakkiyar fuska .   Babu kome hajja ai lafiyar mama ta sa'a wuce aiki muhimmanci bari mu je ga likitan ta .    Bayan dogon bayanin da kamar maimaici ne gare shi akan cutar ƴar ta sa wacce take ɗauke da ciwon Amosanin jini , " da a turance ake ƙiran sa da Sickle Cell Anemia, Ya ɗora da yi masa bayani akan binciken da shi youssouf ya sanya likitan ya yi masa akan wannne asibiti ne mafi kyaun kayan aiki tare da ƙwararrun likitoci da zai iya kai ƴar sa ayi mata aikin da ake sanya ran idan har anyi sa da dacewa masu cuta irin na ta kan iya warkewa baki ɗaya . Fitaccen asibitin nan a duniya da yake ɗauke da ƙwararrun likitoci dake ƙasar amurka ,"Mayo Clinic ," shine asibitin da likitan ya tabbatar da ƙwarewar su akan aikin dashen ɓargo  ga marassa lafiyan da ya shafi manyan cutukan cikin jini . Miƙawa likitan hannu yayi suka yi musabaha lokacin da yake miƙewa akan ƙafafun sa domin barin ofishin . Likitan ya kai duban sa ga mama wacce tayi luf a jikin baban ta tana wasa da adon gaban rigar sa na soji . Madame Safiyya Baskore sommes-nous bien maintenant? pas plus d'injection non?    dariya  tayi kafin ta amsawa likitan dai-dai lokacin da suke ƙarasa barin ofishin ita da baban ta .    oui je me sens mieux maintenant plus d'injections . Dariya likitan yayi yana ɗaga mata hannu alamun ! bye bye !      A hankali ta motsa laɓɓan ta tana kwantar da kan ta kan kafaɗun baban ta   au revoir ! ( Bye ) ..       Assalamu Alaikum kowa da kowa !    Surprise ??  😂 Ina gaisuwa agare ku baki daya masu karatun da suke faranta min wajen Danna dan tauraron nan tare da ajiye min sharhin su a karkashin kowanne shafi na rubutu na,  ina son Sanar da ku cewa ina godiya me dinbin yawa agare ku. Okay ghost readers, Makaho bai San Ana ganin sa ba sai an zungura shi ko ?? 😠 Kun san bakwa kyauta min koh?     Amma ba kome a dai juri zuwa rafi wataran tulu zai fashe,  😂 [9/3, 10:14 PM] +234 806 122 1116: Fikrah writers association MAFARI ( Hargitsin Rayuwa ) Umm'muaz 33 Wannan shafin na bada tukuicin sa baki daya ga " ZULAIHAT RANO " MEELAH " RALIYA GARBA. #I MORE THAN APPRECIATE YOU SISTERS# Bayan an sallami mama daga asibiti sun dawo gida , idan banda lelen ta babu abunda falmata take rabon ta da makarantar ta ma yau kusan sati guda kenan , Domin duk yadda hajja ta so falmata ta tafi makarantar ta bar mata kulawar mama ta ƙiya , gani take daga ta matsa daga kusa da ita ciwon nata zai iya tashi . A zaune suke a falo hajja tana kishingiɗe tana hutawa bayan ta gama ƴan kananun aiyukan ta na safe , Mama tana kalmashe bisa cinyar falmata , wacce take bin duk gaɓoɓin maman tana tausa mata su sannu a hankali , jikin ta sanye da ruwan hodan kayan sanyi na yara mata me adon ƴan ƙula-ƙulai farare , ƙafafun ta a ƙunshe cikin fararen safar ƙafa . Biyamuradi ya shigo falon , a shirye yake tsaf cikin kakin sa na soji , fitowar sa kenan daga sashin sa da yake sabon gidan da ya saya musu wanda ya fi wanda suka fara zaman haya a cikin sa girma da tsari , domin wannan sashi uku ne da shi ƴan madaidaita , sashin da su falmata suke da sashin baƙi wanda ba'a amfani da shi sai kuma sashin biyamuradi da idan ya zo garin yake sauƙa a cikin sa a wasu lokuta , musamman a lokacin da ya tarar da rashin lafiyar mama , wasu lokutan kuwa a hotel yake zaman sa . Mama tana jin sallamar sa ta miƙe daga jikin falmata wacce take ƙoƙarin riƙe ta , Mama ki tafi a hankali kin ga ba wani ƙwarin jiki kika samu sosai ba , Bata kula ba Ta taka da ɗan gudun ta , da sassarfa shima ya ƙaraso ya chafe ta sama ya cillata , Yana juyi da ita kafin ya sauke ta zuwa ƙirjin sa yana dariya , Bonjour papa , ina kwana papa . tace daidai lokacin da take kai hannu tana ƙoƙarin cire hular kan sa , Taya ta cire hular yayi ya ɗora mata bisa kan ta da aka mata manyan kitson kalba suka zubo har kan kafaɗun ta , Bonjour mon cher ," yaya kin ka tashi ? Lafiya papa tace da shi daidai lokacin da take ƙoƙarin sauƙa daga ƙirjin sa , Ya sauƙe ta yana riƙe da hannun ta suka ƙarasa cikin falon , ya samu mazauni kan ɗaya daga cikin kujerun wajen yana gaisawa da hajja wacce ta miƙe zaune daga kishingiɗar da tayi , Kamar yadda ta saba , yanayin ta babu walwala idan har yana waje ta gaida shi , tana riƙo hannun mama wacce take ƙoƙarin ajiye mata hular baban ta a kai , Bata iya hana ta ba sai da ta ɗaura mata hular akan hular da take rufe akan ta wacce take mahaɗin doguwar rigar jikin ta ruwan madara me ɗan nawi saboda tashi da aka yi da ɗan sanyi garin sakamakon ruwan sama da aka kwana yi daren jiya . Shafa fuskar ta mama tayi , kamar yadda yake al'adar su ita da mamar ta . Maama kin yi chau dayawa , Papa ka ga maama na tayi chau , donne-nous des photos , ta ƙarasa zancen tana hayewa kan kujerar da falmata take ta zagaya ta bayan ta gami da sarƙafa hannuwan ta biyu ta wuyan falmatan ta cusa fuskar ta gefen wuyan ta ., Biyamuradi wanda ya fara yiwa hajja bayani game da shirye-shiryen da yake na tafiyar su US , ya juyo da duban sa kan su idanun sa suka sauƙa kan fuskar falmata wacce haƙoranta ke buɗe tana murmushin da yake bayyana farin cikin ta da ganin walwalar mama ya assasa mata , Kamar maganaɗisu ya riƙe shi , ya kasa janye idanun sa daga kan ƴar fuskar ta da komen ta yake ɗan madaidaici idan aka cire manyan idanun ta , Ba tare da ya iya ɗauke ido daga kallon ta ba ya zaro wayar sa daga aljihu , ya juyo baki ɗayan sa ya saita cemara ya haska musu hotuna wajen kala shidda , Da gudu mama ta sake sauƙowa ta dawo wajen baban ta , tana cewa zata ga hoto ? Ta ɗare cinyar sa , Batare da ya sake mata wayar ba ya nuna mata hotunan , da sauri ta sanya hannu tana sake tura huton gaba , fuskar wata ƴar baby me kyau kamar ta ya cika fuskar wayar , ƴar yarinya ce da bata wuce shekaru biyu ba tana tsaye a hoton , A hankali mama ta ɗago kan ta tana duban fuskar sa Papa bebe waye ? Zare wayar yayi daga hannun ta ba tare da ya bata amsa ba, daidai lokacin da hajja ta ke cewa , Wannan yarinyar da surutu kike kamar aku , duk kin bi kin tsare shi da surutu kin hana shi ya yi magana , bayan kuma yayi shirin tafiya aiki , ni zo nan ki zauna na miki tafiyar tsutsa a ƙafar ki . Sauƙa tayi daga jikin sa , maimakon ta tafi wajen hajja , sai ta nufi mamar ta , tana zuwa ta zauna a gefen ta gami da kwantar da kai a jikin ta tayi shiru , Boyayyar ajiyar zuciya Biyamuradi yayi , cikin ran sa yana hamdala da hajja ta katse masa tambayoyin mama , domin Alƙawari ya ɗaukarwa kan sa ba zai taɓa yiwa ƴaƴan sa ƙarya ba , akan duk wata tambaya da suka masa , sai dai ko ya sakaya amsar idan kaifin hankalin su bai kai su fahimce ta ba , amma a yanzu bai shirya amsa ba ga tambayar da mama tayi ma sa . Cigaba da yiwa hajja bayani yayi , inda yake sanar da ita , yana son ranar litinin ya zo su je ayiwa falmata da mama passport , zai fara nema musu visa Idan Allah ya yadda daga sun samu visa shi da su zasu tafi US , da ba zai wuce tsawon nan da wata ɗaya da ƴan kwanaki ba nan gaba , Ba shi da masaniya akan tsawon lokacin da zasu iya yi a chan ,saboda harka ce ta neman lafiya , bai san yadda lamura zasu kasance ba , amma dai visa ta tsawon watanni shidda zai samar musu . Ya ɗora da neman hajja ta masa bayanin duk wasu abubuwan da zata iya buƙata bayan kayan abinci da sauran abubuwan buƙata na rayuwar yau da kullum wanda zai iya kai ta watanni shidda ko fiye da haka , Da farko addu'o'in samun nasara akan abunda zasu nema tare da addu'ar nemawa mama samun waraka tayi ta jerowa , tana jin yadda tausayin su duk ukun ke kama ta , Babban soja , ni ba sai an min tanadin kome ba , saboda ka ga nima wajen shekaru biyu ake nema rabona da ƴan uwa da dangi , dan haka idan har tafiyar ta tashi , bayan kun tafi a washegari nima zan ɗau hanya zuwa nigeria nima naje na sada zuminci na ga ƴan uwa da dangi , shekaru sun fara jaa , mutuwar nan ta yanzu kar ta gifta tsakani ba'a nemi gafarar ƴan uwa ba , idan ya so bayan dawowar ku ko kuwa ma kafin ku dawo sai a sanar min nayi dawowa ta , ai ka ga nima na ribaci lokaci ko kuwa ? Babu shakka hakane hajja , to babu kome idan har tafiya ta kama lokaci yayi sai ki tafi zouwa gida kafin dawowar mu , Allah ya saka da Alheri , ki min duk wasu bayanai na abubuwan da kike buƙata da zaki yiwa mutanen gida tsaraba don Allah .! Toh madallah Babban soja , amma dayake nima a wajen nawa akwai ƴan kuɗaɗe irin waɗanda kake min kyautar su ai ba ma sai na maka lissafin kayan tsaraba ba , idan tafiya ta zo ni da kaina zani nayo ƴar tsaraba ta , A ah hajja , don Allah kar ki ce hakka , irin Alherin da kika mouna a rayuwa ba zamou iya biyan ki ba sai dai Allah shi saka da Alheri , ƙwarai ƙwarai ina miki godiya , ki min lissafi abun da kike buƙata duk zan sa a kawo kome ranar da zaki tafi sai direban da ya kai ki wancen karon ya sake kai ki nagode ! Ni ce da godiya Babban soja ni ce da godiya , Allah dai ya ƙara buɗi , ya ba wa mama lafiya , Ameen ameen hajja ya amsa yana miƙewa , Sashin da suke ya mayar da duban sa , mama har tayi bacci fuskar nan a chakuɗe alamun fushi take , Bai yi mamaki ba saboda sanin ta da yayi da saurin bacci , A hankali ya taka zuwa gaban falmata wacce tayi shiru , tana ɗan shafar kan mama da yake bisa cinyar ta , Fatima ni zan tafi bakin aiki zouwa le lundi zan dawo mu tai à muku passeport , ki kula da mama kar tayi wassa dayawa idan ta ji sauƙi sosai sai ta cigaba da zouwa école . Toh Allah ya kiyaye hanya ,! Ta amsa masa , Ɗan jim yayi a tsaye yana ƙure mata kallo da buɗaɗɗun idanun sa , hular ta shi ta karɓi yar zagayayyar fuskar ta me ɗan haske kaɗan , ji yake kamar ya bar mata hular a kan ta yayi ta kallon ta a haka , Jin yayi shiru kuma ta san da tsayuwar sa a wajen ya sa ta ɗan dago kan ta , tana sake haɗe fuska , Gyaran murya yayi ganin yadda tayi kicin-kicin kamar zata fashe masa da kuka . Fatima donne moi mon chapeau! ( miƙe min hula ta ) Ya furta hakan yana sake rage amon muryar sa , Falmata wacce tsayuwar sa akan ta da idanun sa da take ji suna mata yawo a jiki tamkar suna mintsinin ta ya sa ta diririce ta gaza fahimtar me yake cewa , ba wai dan bata jin yaren da yake yi ba , Mama bacci take . ta ce da shi tana fatan ya bar kan ta A hankali ya sunkuyo har tana iya jiyo hucin humfashin sa a fuskar ta  ya kai hannun sa guda ya zare hular sa dake kan ta , ya mayar kan sa . Na tafi Yace da ita yana juyawa ya bar wajen . Wani irin yanayi ta ji a jikin ta uwa wacce aka zubawa ruwan sanyi , har ga Allah ta mance da hular sa da take kafe a kan ta , Runtse idanun ta tayi da ƙarfi tana jin yadda zuciyar ta ke bugu . Hajja wacce duk abunda ya faru akan idanun ta tana iya hango su daga inda take . auho ! aikin banza ihu bayan hari , da kike wani runtse ido kina wani kawar da kai ya ƙadangariyar gobara , ai wallahi ni dai na daina saki a hanya kan sha'anin auren ki , tsakani na da ke ido ,! Ace wai tsawon shekaru fiye da biyar kin kasa zama cikakkiyar matar gida , ke kenan ɗaurewa miji fuska kina muzurai , zauna nan yarinya za'a yi bake lokacin da Babban soja ya gaji da halin ki ya sillo auren sa babu ni a masu yi miki dannar ƙirji , ko muƙamuƙi ba zan danna miki ba . Cikin rashin kulawa da zantukan hajja wanda falmata ta riga ta saba da jin makamantan su , tace Hajja ta me kika ce ? Abunda wancan yace , shi nace Ta amsa mata tana shirin miƙewa daga inda take tana cigaba da mita , Ƙatuwar mace kamar ki ace wai har yau tana da miji amma bata san amfanin sa ba sai rainon ƴa ,? Ai ni ina kamar ki nayi aure na na biyu ma , Ki ka ce me hajja ta ban ji da kyau ba ?? Na ce gidan ku ! Ta amsa mata tana ƙarasa barin wajen Murmushi falmata tayi domin ta san ta ƙular da hajja , Cikin ran ta tana juya maganganun hajja , Ban da abun hajja shi mutumin da kullum.take kumfar baki akan a kula da shi ɗin , shi ya taɓa nuna wata alama ne na kasancewar ta matar sa ? Tsawon shekarun auren su a tun bata san me takamaimai kalmar auratayya ke nufi ba , har ta zo ta san me ake nufi da aure ta hanyar malamar da take koyar da ita wacce a farkon fara ɗaukar darasi a wajen ta take yawan yi mata bayani akan auratayya a addinance da yadda mace zata kula da kan ta da mijin ta ta fuskar auratayya ba tare da kunyar kome ba cikin rashin sanin ta hajja ce ta yiwa malamar bayanin ƙarancin ilmi da wayon falmata ta kuma roƙi da ta dunga mata darasi na musamman akan auratayya , A hankali yau da gobe ta fahimci manene aure , matsayin miji a gun matar sa da matsayin mata a wajen mijin ta , Ta shiga ruɗani na sosai da har kawo yau bata fita daga cikin sa ba , " yaushe yakaka da Baban mama suka yi aure ?? Ita ba ta san lokacin ba kawai jin yakaka tayi da cikin mama . Akwai tsoro me tafe da son bada kariya tare da kyautata zato ga ƴar uwar ta yakaka , haɗi da son tsaftace mama shi yasa a duk lokacin da tunanin hanyar da aka bi aka samar da mama ya taso mata , take yaƙar tunanin da ƙarfi da yaji , bata son wani abu da zai aibata yakaka ya raɓi tunanin ta , Kewa tare da ƙaunar ƴar uwar ta bai ragu ba ko kaɗan a cikin ran ta sai ma zurfafa da yake sake yi yayi mata ƙaton miƙi a cikin rai . Rashin son suyi zaman auratayya irin na sauran ma'aurata da Biyamuradi ya nuna tsawon shekarun bai taɓa damun ta ba , Hasalima ta fi son hakan . Zaman mama take , tana rayuwa ne a ƙarƙashin sa kaɗai domin mama , za kuma ta cigaba da tsayawa ɗauke da auren sa a kan ta har abada muddin tana tare da mama . **** Daga niamey kai tsaye maraɗi ya wuce , bayan isar shi faɗa ya kai gaisuwa , kai tsaye ɓangaren sa ya nufa ba tare da ya shiga cikin gidan su wajen hajiya umma ba , yasan yanzu tana tare da jama'a masu neman taimako da ƴan barandar ta , sai zuwa yammaci zai shiga wajen ta zuwa lokacin ƙafa ta ragu a sashin nata .. Tattaki yayi zuwa sashin sa da yake bigire guda na gidan , bayun da suke kai kawo a fada su na ta kai gaisuwa bayan waɗanda ke take masa baya tun daga ƙofar fada . A bakin sashin sa suka jaa tunga saboda a tsarin sa bayi maza basa shiga ɓangaren gidan sa da matan sa ke ciki . Yana sanya ƙafar sa a cikin gidan ya ji wani yanayi marar daɗi na lullubar sa , hakan kuwa yana da nasaba da rashin daɗin zama a gidan da yake ji har kullum ya kuma rasa dalili . Taku ya fara yi da nufin isa sashin gimbiyar ta shi maimouna . Sai dai ƴan hannuwan da ya ji sun riƙe masa ƙafafun sa su suka sanya shi ya maida ganin sa ƙasa ,! Yumna Ya furta yana ƴar dariya tare da kai hannu ya ɗauki ƴar yarinyar da take ta yi masa dariya , ya ɗaga ta sama ya cilla ta tana ɓangala masa dariya . Rungume ta yayi a jikin sa lokacin da yake maida duban sa kan mamar ta wacce take ƙarasowa wajen fuskar ta ɗauke da murmushi , a shirye take tsaf , ba wata shahararriyar kwalliyar fuska tayi ba illa jikin ta da yake kiruf a rufe da babban mayafi tun daga wuyan ta da ya sha ado da tufafi irin na alfarma ,wanda ya amshi zubi da tsarin jikin ta na samɓaleliyar mace me zubin matan fulanin usul . Janye idanun ta tayi daga cikin nasa kamar koyaushe da bata iya jurar ganin cikin idanun sa duk kuwa da tsawon shekarun da suka shafe a matsayin ma'aurata , Barka da zouwa Baban Yumna , da fatan ka isso lafiya ? Lafiya mun same ku lafiya ? Yaya Yumna ? Ga ta tana lafiya , Ɗan shiru suka yi kafin ya katse shirun da tambayar ta Ina kuke da noufin zouwa da hantsi hakka ?? A ɗan ruɗe tace , zamu shiga fada gaishe da hajiya umma , Baza ku fita yanzou ba umma na tare da jama'a da wannan lokacin bani son idanun jama'a bisa ga kan ɗiya ta , ko dai ki bar ta ki tahi ke ɗai , ko kuwa ki bari da sanyin la'asar kun tahi tare . Ko kusa baza ta so ƴar ta ta gifta ta kurkusa da shigifar gimbiya moumuna ba bare har ta taka ƙafafun ta cikin wani al'amari da ya gifta a tsakanin su me girma , wanda ya tarwatsa takaitatcen zaman daɗin da suka fara gudanarwa a tsakanin su , daga nan aka yi walƙiya kowa ya shaida kowa , yayin da daga lokacin ta fara bin irin takun gimbiya moumuna da nazari , nan ta fahimci dayawa daga cikin boƴaƴƴun fuskokin ta masu cike da abubuwan al'ajabi tare da sarƙaƙiya da baki yayi kaɗan wajen furta su ga wani har sai idan wannnan mutumin ya ga kome a idanun sa . Hakan ya sa ta rufe kome ta haɗiye a cikin ta , ta kuma killace kan ta da ɗiyar ta daga gimbiya moumuna da ƴan barandar ta doumin ita ɗin ai gubba ce ga rayukan alhalin masarautar maraɗi ! Da sauri ta miƙa hannu tana ƙoƙarin amsar ƴar ta daga gare shi Mun hakure zouwa yammaci kamar yadda ka faɗi mouna Biyamuradi . Janye yumna yayi ya hana ta ɗaukar ta , a hankali ya kamo hannun tare da  sarƙafe ƴan yatsun sa a cikin nata hannun yana jin yadda taushin hannun ke tado masa da yanayin da yake ta dannewa tsawon satika , " muryar sa tafe da amo marar ƙarfi yace Mu tai ki ciyar da ni abounci na taho tare da yunwa me tsanani . Ƙoƙarin zare hannun ta take tana satar kallon sashin gimbiya maimouna , Cikin sa'a idanun ta ya sauƙa akan gnala shugabar bayin sashin gimbiya moumuna ta na abunda yake goge gilashin falon gimbiyar ta ciki a zahiri , wanda tashin farko siyama ta fassara abunda take da ɗaukar rahoto Toh Biyamuradi , amm... Shitt yace mata lokacin da yake jan hannun ta zouwa sashin sa kai tsaye da yumna saɓe kan kafaɗar sa ta dama tana ƙoƙarin ɗauke hular kan sa , Suka fara taku tare da masaniyar yau wajen ta ya kamata ya kwana a tsarin ƙwanakin girki . Gimbiya moumuna wacce tun isar sa fada ta samou labarin zuwan sa , inda bata yi ƙasa a guiwa ba ta tashi shirin tarɓar sa , Ta tashi hankulan bayun ta da aikin gyara gida wasu kuma na haɗa mata ruwan wanka tare da fidda mata kayan da zata sanya a jikin ta , Zuwa shigowar sa gidan ta fito daga wanka ta fara shiri , yana dosar gidan saƙo ya iso mata , hakan ya sa ta miƙe daga gaban mudubi ta ƙarasa gaban babban window na ɗakin ta dake sama ta raba labulen biyu daga inda take ta hangi kome da ya wakana tsakanin sa da siyama . Wani irin tuƙuƙi take ji yana taso mata daga cikin rai har tana jin ɗacin sa a maƙogoro . Meyasa ne wankin hula ya kai ta ɗare har tsakiyar sa ?? Lamarin da suka yi hasashen yiwuwar sa a watanni zuwa Shekara bayan zuwan ta masarautar maraɗi , sai ga shi shekaru har sun fara ƙoƙarin haurawa kirgen yatsu biyar ?? Wacce iriyar mummunar rashin sa'a ne gare su haka ?? Wanne sirri ne da yake boye cikin duhu da ya zamto shamaƙin da ya shiga tsakanin ta da cikar burin ta ?? Menene shi da ya wuce tasirin ƙarfin su ?? Tattare labulen tayi ta cukuikuye shi a tafin hannun ta tana jin kamar tayi girgiza ta fasa bango ta dira a sashin yarima youssouf ta kaddamar da manufar ta .. Ranki ya daɗe kƴakya..... Bata bari gnala ta ƙarasa kalmomin ta ba wacce ta shigo ta durƙusa daga bayan ta , Da hannu ta dakatar da ita , Ayi gaugawar shiryawa Biyamuradi abincin sa a aika da shi shiyar sa ., Ke zaki miƙa abincin da kan ki daga nan kin kawo mi ni labari na lamarin da ya auku gaba gare ki . Allah ya huci ran gimbiya ƴar sarkin nahiyar mu maigirma oumarnin ki shine abun bi .! da shigar su sashin nasa da yake me matuƙar girma , da tsari tare da wadatar tsaftar da ta haifar da kyakkyawan yanayi a wajen , Ya zauna bisa ɗaya daga cikin kujerun falon nasa , yana sauƙe yumna kan kafafun sa , siyama wacce ta saɓule mayafin ta ta ajiye a gefe ta sunkuya tare da yin gurfano a gaban sa , cikin nutsuwa ta kai hannuwan ta tana kunce masa igiyar takalmin sa tare da zare masa shi a hankali , Ɗan kiɗan da wayar sa ta yi dake nuna alamun shigowar saƙo ya sa shi zaro wayar daga aljihun sa ,    Lokacin da take ƙoƙarin karɓe hular sa dake hannun yumna ta ƙi bada hular ,     Ki bar mata hular mana , kin ka sani ko ɗiya tayi gadon baban ta ?    Da murmushi bisa fuskar ta ta wuce sama domin ajiye masa takalman sa , ta zo ta fara yi masa shirin girki .    Saƙon gimbiya maimouna ne mai ɗauke da tsararrun kalamai na barka da zuwa ƙarshe take sanar da shi ta bada saƙo a kawo masa ,   Fita yayi daga wajen adana saƙon yana shirin ajiye wayar hoton da ya ɗauke su ɗazu ya bayyana a fuskar wayar, Ƴan yatsun sa ya sa ya jawo hoton ya cika wayar ya na nutsar da idanun sa kan fuskar ta me ɗan haske kaɗan da  take ɗauke da wani sirri me tasirin da ya zarce a ƙira shi kyau , fatar ta suɓul-suɓul babu wasu ƙurarraji bare tabbuna manyan idanun ta da yankan su yake a tsaye da ƙwayar baƙi na cikin su me girma ne sosai , suna da ɗaukar hankali ta yadda ko yaya ta juya su sai mutum ya gan su ,   har kullum yana dogon tunani akan son sanin me ya makanta su ??   A hankali yayi ƙasa da hoton zuwa kan bakin ta da haƙoranta suke a buɗe tana dariya ,     Tsintar kan sa yayi da murmusawa, ya kai babban ɗan yatsan sa yana shafar fuskar wayar daidai zagayen ɗan bakin nata ,      lokacin da ya tuno da yadda take haɗe fuska ta tsuke bakin , duk idan ta ji motsin sa a waje , ta takura kan ta ta gaza walwala ,,   Kiyi haƙuri fatima ni ma ba zaɓi na bane irin rayuwar da muke gudanarwa a tsakanin mu a matsayin ki ta iyalina ,girman laifi na ya sa na gaza yin wani yunƙuri ,  ni ɗin me laifi ne a gare ki da duk ranar da gaskiya ta bayyana wataƙila baza ki yafe min ba , hakan ya sa na jinkirta miki har zouwa lokacin da kome zai bayyana agare ki , da na tabbatar ranar ta na zouwa , lokacin kike da zaɓi na zama da ni ko bari na bisa ra'ayin kan ki ,      Kiyi haƙuri Fatima zahra ina jin kunyar ki .       Ƙwanƙwasa ƙofar da aka yi ya sa shi kai duban sa ga ƙofar tare da mayar da wayar sa cikin aljihu    Daidai da ƙarasowar siyama wajen wacce kalaman sa na ƙarshe suka sauƙa cikin kunnuwan ta ,     Suka yi sanadiyyar harɗewar takun kafafun ta tare da sa zuciyar ta yin tsalle .   Wacece fatima ? Wanne matsayi ne gare ta da har Biyamuradi ke neman afouwar ta ? Shin laifin me ya aikata mata ?      Ruɗanin da ta afkawa ya hana ta tsinkayar kalaman da yake mata sai da ya ɗan ɗaga muryar sa da ƙarfi .   Siyama ki buɗe kofar nan saƙon maimounatu ne ya iso ,     Ba tare da ta amsa ba ta taka tana nufar ƙofar , cikin ran ta damuwa goma da ishirin ta san sarai saƙon ko na menene, abunda maimounatu ta saba yi mata ne a koyaushe , shine yau ma ta maimaita . Tana buɗe ƙofar tayi arba da gnala tare da wasu bayu biyu hannuwan su riƙe da manyan farantai da aka rufe su da tumaƙasa irin na alfarma ,    Ajiye faranta suka yi tare da yin gurfano a gaban ta ,   Ranki ya daɗe barka da fitowa !  saƙo ne daga gimbiya tace a shigar da kaɓaki ga maigirma yarima .    Fuskar ta a ɗaure ta ce Ki je sashi na yanzu yanzu ki ƙira min Rakiya ku zo tare ! Da sauri Gnala ta miƙe Ba ke ba .   Tace da kaushin murya   Ciki sauri ta koma ta tsugunna Ke tashi ki je ki taho da Rakiya    Tana nuni da ɗayar baiwar . Cikin ƙasa da mintuna uku sai ga su tare da wata yarinyar mace da zata iya zuwa sa'a ga siyamar ,    Ranki ya daɗe uwargijiya ta . Rakiya ki ɗauko waɗannan farantan ki biyo ni da su ,     Ta furta haka tana juyawa ciki Rakiya ta bita ɗauke da faranti guda , kafin ta dawo ta ɗau sauran da ɗai ɗaya ta shiga da su ,      Tana gama shigarwa ta fito gami da jan ƙofar , tana iya jiyo lokacin da uwargiyar ta ta murza ɗan mukulli , Kallon kallo suka yi tsakanin ta da gnala , kafin ta ratsa ta tsakanin su tana wucewa kan ta a ɗage bakin ta ɗauke da ɗan siririn murmushi ta fara rere waƙar da ta zo kan harshen ta a dai-dai lokacin   Aiki yayi kyau , tunda gida ya gyaru tsaf-tsaf ?    Allah kawo ran albashi mui fatantamawaaa . Na ku nawa ne ?  nawa kuka ɗauka a wata ɗaƴa ? In an bincika in an bibbiku da ɗai ɗai , har ma'aikatan zaria har ku na fi kowa ,  ɗan ɗan ɗaraɗanɗan .........   Da kallo suka bi ta tsaurin idanun Rakiya ba sabon abu bane a wajen su duk kuwa da cewa su sun fita daɗewa a gidan domin ita sabuwar ƴar aiki ce da ubbo ta kawo wa siyama tun daga jahar kanon nigeria .    Bata da kunya , bata kuma da tsoro ko kaɗan fallalliya ce ta ƙin ƙarawa . **** Fuskar ta babu walwala ta zuzzuba masa duk abincin da yake wajen akan wani ɗan faranti me ɗaukar ido , ta tanadar masa duk wasu abubuwan da ta san zai buƙata a wajen cin abincin ta mike tana barin wajen bata bi ta kan yumna ba wacce ta ɗau murfin wani ɗan kwano tana miƙa mata tare da yi mata gwarancin ta na yara , ta wuce ta tana nufar sama ,....    Ta ƙasan ido ya bita da kallo , ganin fushin ta a duk lokacin da maimounatu tayi masa aike ya haka ba sabon abu bane a wajen sa , siyama tana da zafin kishi shi da kan sa ya san haka , saɓanin maimounatu wacce tarin hikimar ta tare da wayo ya sa bata saurin bayyana kishin ta a fili har a fahimta ,   Shi da kan sa yana mamakin yadda ake maimouna take sanin zuwan sa maraɗi tun kafin ya iso gida ,Ko da kuwa bai sanar da kowa zuwan nasa ba , ya haka da yayi zuwan bazata , zai zo ya tarar tayo shirin tarɓar sa na musamman kamar daman ya sanar da ita zuwan sa ,  hakan ya sha faruwa ba sau ɗaya ba ba sau biyu ba maimouna tana iya sanin duk wani motsin sa a cikin maraɗi , wanda shi ya ɗau hakan a matsayin tsantsar kulawa , to ina laifin wanda ya kula da lamarin ka ??      Cigaba yayi da cin abincin sa cikin nutsuwa , yana jin yadda hoton fuskar falmata ke yawo a ran sa har ya hana shi jin daɗin cin abincin so yake ya sake kallon ta, dan haka ya sake ɗaukar wayar sa ya buɗo hoton , yana sake kallo lokaci lokaci yana cin abincin sa tare da sanyawa yumna a nata bakin . Abuja Yau garin an tashi da hadari bakikkirin kafin zuwa hantsi ruwa ya fara sauƙa kamar da bakin ƙwarya , Yakaka ita kaɗai ce a gidan ƙwal , saboda samira bata kwana a gidan ba tun jiya da yamma suka fita tare da Alhaji Gali . Gaba ɗaya bata jin ɗaɗin yanayin da ta ke ciki , gidan yayi shiru dayawa duk da dai ba shi da girma sosai , zaman shirun ya sa tunaninnika yi mata dirar mikiya , cikin kwanakin nan tunanin falmata da mama ya matsanta mata , ko dan karatun da ya ɗan tsagaita mata ne ? Amma koyaushe cikin tunanin su take ,    Yaya suke ? , ta san duk sun girma Falmata yanzu shekaru ishirin ne da ita babu ƴan watanni yayin da mama ta haura shekaru biyar , Tana begen ganin su duk da cewa samy baby tana tabbatar mata da lafiyar su , a cewar ta suns waya da Rahima wacce take sanar da ita halin da suke ciki , har ma ta ce yaya doctor ya sa su a makarantu , sai dai duk da haka tana son jin ko da muryar su ne amma anty samy ta hana a cewar ta ji daga garesu zai iys kawo tsaiko ga harkar karatun ta , zata yi rauni ta gaza maida hankali ga karatun ta , da jin hakan ya sa ta haƙurewa jin su , Ta bari har sai bayan kammaluwar karatun ta da samy baby ta mata alƙawarin zasu tafi maidugurin tare kamar yadda ta ɗauko ta ƙafa-da-ƙafa , ta je ta taya ta wanke kan ta a wajen falmata , yaya doctor , rahima da ma baba , ƙarshe kuma ta rungumi ƴar ta da ƙanwar ta su dawo tare nan .! Duk da cewa a farkon zaman su da samy baby ta kasa sakin jiki da ita ganin irin yAudarar da tayi mata ta rabo ta da maiduguri da ƴar uwar ta , sai ta kasance cikin ɗari-ɗari da ita tana tunanin ko zata yi yunƙurin cutar da ita sai dai abunda ya sa ta saki jiki bai wuce yadda lokaci yayi ta tafiya ba tare da ta ga wani sauyi na gallazawa , tilastawa ko ɓatanci daga samy baby ba ,sai ma hidima da take yi da ita tare da kyautata mata fiye da zaton ta , Tsawon shekaru biyar da suka yi tare samy baby ke ɗauke da nawin duk wasu buƙatun ta na yau da kullum , cin ta shan ta suturar ta kuɗin magani da na karatun ta duk ta dalilin samy baby ta same su kuma masu kyau masu inganci da suka taimaka mata ƙwarai ta fannin yin rayuwa me cike da inganci da isasshiyar lafiya tare da nasarar kammala karatun ta , Dan haka a sannu sannu samy baby ta mantar da ita girman laifi tare da yaudarar da tayi mata , a ƙarshe ta sake shirya mata sabuwar ƙaryar cewa suna waya da rahima , falmata da mama suna lafiya , wanda a zahiri ba gaskiya bane , hasalima rabon ta da shiga maiduguri ita ma ya doshi shekaru huɗu , kuma bata tare da number rahima , ba ta ma sake biyawa ta kan rayuwar bayin Allah biyun da ta raba su da garkuwar su ba , Ta tsara haka ne saboda yakaka ta sau jiki ta zauna tare da ita , yadda gaba zata cimma manufar ta hankali kwance ba tare da yakaka ta sake tayar mata da bori ba ! Sai dai kamar yadda suka alƙawarta lokaci ya zo da zasu maiduguri , idan ya so bayan dawowar su sai ta shiga jami'a kamar yadda samy baby ta sake ƙwaɗaita mata a cewar ta jami'a shine mataki na gaba da ya dace da yakaka , duk a ƙoƙarin ta na son janye ta zuwa kan turba irin ta ta , da take ganin fa a yanzu lokaci yayi . Ƙofar da ake bugu da ɗan ƙarfi ya sanya ta firgita ta dawo daga nisan tunanin da ta tafi . Duban agogo tayi ta ga ƙarfe goma sha biyu na rana ,   Fitowa tayi da nufin zuwa ta buɗe ƙofar da take hasashen dawowar samy baby .    Har lokacin ana yayyafi yif-yif da alamun yau yinin na marka-marka ne .      Da ɗan gudun ta ta ƙarasa bakin ƙofar ta zare sakatar ƙofar ba tare da ta waiwaya ba ta juya da gudun kar ruwan sama ya taɓa ta tana cewa    Sannu da zuwa anty samy .    Sai da ta tsallaka kan Balcony tukun ta juyo ,      A tsorace ta kai duban ta ga mutumin da yake tsaye a maimakon samy baby ,     Saurayi ne dogo wankan tarwaɗa yana tsaye ya zura hannun sa cikin wondon jikin sa , idanun sa sakaye cikin wani kwafcecen baƙin gilashi da kallo ɗaya za'a masa a fahimci rangwamen mutumcin dake tare da shi .    Juyawa tayi da sauri ta tura ƙofar falon ta shiga sabods tunowa da tayi da riga da wondon da suke jikin ta na bacci da duk da cewa basu kama ta ba ko kaɗan amma kaya ne masu tsantsi.    Kai tsaye ta shiga ɗakin ta ta fara bincikar hijabin ta ,    Sai dai hannun da ta ji ya sauƙa a ƙafaɗar ta ya sa hantar cikin ta kaɗawa ,   Da sauri ta jaa baya har tana gwaruwa da jikin wardrobe ,   Idanun ta ya shiga cikin na saurayin da ta bari a waje ,     Anty samira bata nan ta furta haka , muryar ta na karkawa , lokacin da take ƙoƙarin zira hijabin da ta samu nasarar ɗauka ,    Riƙe hajibin yayi da hannun sa ɗaya , yayi amfani da ɗayan hannun sa wajen zare gilashin idanun sa , mitsitsin jajayen idanun sa da suka sake shigewa ciki-ciki suka bayyana , yana bin ta da wani shu'umin kallo    Da muryar sa irin ta mashaya , yace   Wa yake ta samira tsahuwar guzuma ?    Ga kamar ki gorgeous , ya ƙarasa zancen yana kai hannu zai taɓa kumatun ta ,    Da ƙarfi ta make hannun sa gami da saurin zura hijabin ta ,    Ni ba ƴar iska ba ce kar ka sake taɓa ni , ka fita min daga ɗaki ,   Ɗan baya ya jaa yana yarfe hannun sa da ta buge bakin sa a ɗan buɗe alamun mamaki ,    Baby har da duka ?? Bata kula shi ba ta haura ta kan gadon ta ta dira tana nufar ƙofa , sai dai taku biyu kawai tayi ta ji ya kamo ta ta baya ya haɗa bayan ta da ƙirjin sa ya ɗaga ta ciɗak , ya shiga juyi da ita ,     To tunda wasan tsale tsalle kike so bari na miki hajijiyar ƙauna .     ya furta haka yana ɓaɓɓaka dariya . Tun ƙarfin ta ta fara ihu tana wutsil-wutsil da kafafu tare da ƙoƙarin son ɓanɓare hannun sa da ya zagaye cikin ta da shi , A guje samy baby da tun a tsakar gida ta fara jiyo ihun yakaka ta ƙaraso cikin ɗakin .     Kai kamal meye haka ?  kayi hauka ne ?? Dallah sauƙe ta .    Ba tare da ya sauƙe ta ba ya ce   Ke dallah kauce ki ɗan sakayo mana ƙofa zamu buga ƙwallo ne ni da wannan me zafin kan da tayi gigin duka na .   Ƙarasowa tayi ta jaa hannun sa ,    Kamal kar muyi haka da kai dan Allah ka sauƙe ta , ƙanwa ta ce fa , yaushe muka fara ƴar haka da kai mutumina ??   A hankali ya sassauta rikon da yayi mata kafin ya sake ta tana jin ya ajiye ta ta fita a guje , ƙafafun ta ko takalmi babu ,   Kallon baka kyauta ba samy baby ta wurga masa kafin ta ja ƙaramin tsaki , Kai dai kamal anyi tantiri ɗan iska , to bari na faɗa maka wannan haja ce me matuƙar tsada ba irin taku ba ce domin kuwa sabuwa ce fil , ba'a riga an shiga kasuwa da ita an daka mata wawa ba ,    Ba ta wasa bace na san a ɗan abunda ya shiga tsakanin ku a yanzu kaɗai ,laushin fatar ta da ka taɓa ya isa sanar da kai irin maɗuɗan da zasu taho ta hanyar ta muddin ta shiga kasuwa .      Ƙafar sa ɗaya dake sanye da wani ƙwamemen takalmi sau ciki ya ɗaga yana tokare ta da jikin gadon yakaka . Ni kuma kin san maƙudan da kike faɗa ba matsala ta bane , ko ruwan su kike so nayi miki kin san zan iya , muddin zan mayar ƙwaɗayi na akan wannan nunanniyar gwandar , nawa kike sa mata kuɗi ??   Two Million Naira    Ta furta cikin gatsali Bani account number da zan zira miki su ,      A ɗan jirkice ta dube shi cikin ran ta tana son ƙure shi , domin kuwa duk da sanin da tayi wa kamal na shahararran ɗan masu hali da iyayen sa suka gama gurɓata tarbiyyar sa , ya zama tamkar ɗan taure wajen bibiyar mata , manya da ƙanana kyakkyawa da mummuna shi baya zaɓe kawai dai idan ran shi ya biya ya samu ya maida mugun yawu shikenan kuma bai ƙara bi ta kan mace , bata zaton wasan sa da kuɗi ya kai ya haka .    A ɗage ta karanto masa account number da suna , cikin abunda bai gaza mintuna biyu ba sai ga wayar ta dake cikin jaka ta ɗau ƙara , Jikin ta na mazari ta fiddo wayar ta duba ,    Alert  ne na adadin kuɗin da ta buƙata cif .     Ɗan wara ido tayi da sigar mamaki , sai kuma ta kaɗa idon cikin yanayi na shanye mamakin ta irin na gogaggun matan bariki .     Babu shakka ka ɗau haja me girma , kuma na san baza ka yi wadarai da ita ba , yaushe kake buƙatar ta ?    Haɗe fuska yayi kafin ya watsa hannu    Ka duba wannan da wata maganar iska ? Irin waɗannan kuɗaɗen da na cire har sai kin min iyaka da ita ? Ai yadda ta sani haɗiyar mugun yawu dole daren yau na fanshe kuɗi na , daman ga gari ya ɗau sanyi yanayi ne na shiga daga ciki da sauri . Ta saki Wata dariyar da take bayyana farin cikin ta akan kuɗaɗen da ta samu da dama tana tsakiya da buƙatar su ,    Alhaji kamalu ,  to baka da damuwa ,  yanzu ka tafi , sai ka aika mun address ɗin da kake son na kai maka ita ni da hannun na zan miƙa maka ita anjima da dare ,   Kasan na faɗa maka sabuwa ce bata harkar nan to sai na maka yaƙin shawo maka kan ta , Ɗaga kafaɗa yayi cikin nuna halin ko oho ,      Ni dai ki tabbatar kin mata Wankan irin yadda ya kamata    Ya ƙarasa zancen yana kashe mata ido ,     Alhaji kamalu , kar ka ji kome .daren yau na kai ne a sama . Yakaka wacce take zaune dirshan a cikin ruwan sama ta jikin bangon ɗakin ta ta baya  ,   Ta kai hannuwan ta duk biyu ta toshe bakin ta a ƙoƙarin ta na hana kukan da take fitowa sarari kar su samy baby su ji , kamar yadda duk zantukan su ya ratsa kunnuwan ta .   Ashe daman anty samy yaudarar take akan kome , ashe burin ta ta tsundumata cikin irin rayuwar da tunda ta fahimci girman saɓon da ake aikatawa ta hanyar zina take yi mata addu'ar Allah ya sa ita ma ta tuba ta daina , Manufar ta ashe ta mayar da ita ga aikata zunubin da tayiwa ubangijinta Alƙawarin ta daina baza ta sake ba ! Ƙuka take da hawaye wani na korar wani , tana jin yadda tsoro ke mamaye ran ta , tsoron kowa da kome , tsoron sake yin zina ta hanyar tirsasawa , Takurewa tayi ta sanya fuskar ta tsakanin ƙafafun ta , sanyin ruwan da ya ɗan sake dawowa da ƙarfin yana ratsa ta ta hanyar jiƙa kayan jikin ta . Assalamu Alaykum . Gaisuwa tare da fatan Alkhairi a gare ku baki daya! Nagode.                  Fikra writers association MAFARI ( Hargitsin Rayuwa) umm'muaz 34 Fiye da awa ɗaya Samy baby ta kwashe tana shirya Yakaka , wacce ta sha fama da kanta kafin ta iya tsayar da hawayenta batare da bari Samy baby ta fahimci cewa ta san manufar ta ba , Wacce ta shagaltu wajen shirya ta tana jaan ta da hirararrakin da suka shafi jin daɗin duniya , wankan da kansa so tayi ta wanke ta sai dan ganin ba fuska ya sanya ta tsayawa daga bakin ƙofar banɗakin tana sake jaddada mata ta fa yi wankan nan siral ta fita , domin inda zasu tafi waje ne na manyan ƴan gayu kar ta sake tayi abinda zata jawa kan ta raini ,   Daga cikin banɗakin nan ta ci kukan ta a ƙarshe ta tattara duk wani tunani nata da Allah ya mata baiwar sa ,ta matse ƙwaƙwalwar ta, ta haɗa kai da bango akan tunanin hanyar da zata bi ta samarwa da kan ta mafita . Ƙarfe baƙwai na dare suka fita a motar Samy baby dukkanin su sun ɗau kwalliyya ta gani a faɗa , Duk da fuskar Yakaka a tamke take da bayyanannen ɓacin rai hakan bai hana kyaun da tayi ratsowa ba , dai-dai tana karya kan motar ta fito kan titi sosai Samy baby ta dubi sashin Yakaka a kaikaice ,    Yanzu ke Yaks meye haka ? Dan asara akan na hana ki saka wannan uban barigizan hijabin naki shine kike wannan ƙuncin ? Mts! Ji wannan ƙatuwar jakar da kika ɗauko kamar wata wanzamiya na faɗa miki bata dace da ƙwalliyar nan ba , ƙwalliyar nan taki ba ta babbar jaka bace ta ƴar ƙaramar jakar hannu ce amma kin ƙi ji , ai daman ɗan ƙauye sai ya shekara hamsin a birni yake barin ƙauyenci da gidadanci , ke kika sani sautun mahaukaciya ! Ta danna motar da gudun gaske suka cilla kan titi cikin manyan unguwannin abuja da ko sau ɗaya Yakaka bata taɓa kai ƙafar ta bigiren ba tun zuwan ta garin . Bata cewa samy ƙala ba illa sake rungume jakar ta da tayi wanda a ciki ta saka hijabinta da niƙab ɗin ta , ƙwaƙwalwar ta a hargitse take da sabon tsoron da yake mamayar ta , Ƙofar wani tafakeken gida samy baby ta tsaya tare da zaro wayar ta ta latsa lamba , bugu ɗaya ya ɗauka Gamu mun iso tace tare da sauƙe wayar daga kunnen ta , ba'a yi mintuna uku ba sai maigadi ya buɗe musu ƙofar gidan , samy baby ta danna kan motar a hankali shigar su gidan yazo dai-dai da ƙaruwar firgici a fuskar yakaka , saboda girman gidan da ya wuce hankalin ta ga fitulu da suke a watse birjik a harabar gidan haske ya wadata tamkar tsakar rana , Gefen wasu tsirarun motoci da basu wuce guda shida ba samy baby ta ajiye motar ta , Muje Yaks , A tsorace ta fito tana bin gidan da kallo , ba tare da samy baby ta kula ta ba tayi gaba , cikin jaan ƙafafu ta bita a baya maƙale da jakar ta , suka dumfari katafaren ginin da yake tsaye a gaban su , Babu yalwar mutane a babban ɗakin hutawar da suka shiga ,  mata da mazan da suke harkokin su a wajen babu wanda ya kula su , Samy baby ta jagorance su suka zauna , basu jima da zama ba aka murɗo ɗaya daga cikin ƙofofin da suke ta cikin falon aka shigo , Kamal ne ya shigo yana ɗan gama hanya ya ƙaraso tare da sakin jiki ya faɗa kan kujerar kusa da yakaka , rigijib ! a tsorace ta miƙe tana raba ido .    Idanun sa da suka yi nawi saboda kayan mayen da ya ɗibga ya ɗaga ya watsa mata wani kallon ƙasƙanci , Ke wai ji mana , ya kike wani safurewa haka kina wani ƙoƙarin waskewa , ?  Kamar baki da sanin cewa na biya kuɗin ki , zo nan na fara  morar kuɗi na dallah Ya miƙa hannu ya fisgota ta koma da ƙarfi ta zauna , Ganin sa ya mayar kan Samy baby Yane to yawa kike fa,  Zaman me kike ?  Ko kina neman me tayi ne ? Nan duk suna da chicks ɗin su dan haka ki ƙara gaba ,.. Ke kuma zo muje ki fara tausa min gaɓɓai da waɗannan tausasan hannuwan naki tuɓus-tuɓus , wayyo laushi!      Ya fisgi hannun Yakaka suka miƙe tsaye , Fuskar samy baby ta kalla , idanunsu suka gauraya cikin na juna ,   Ga mamakin samy baby ba kamar yadda ta zaci zata ga hawaye a idanun yakaka ba , saɓanin ta idanun ta a bushe suke ƙyamas ,ɗauke da wani irin yanayi wanda yayi tasiri ƙwarai wajen rage mata kuzarin tashi ta bar gurin kamar yadda aka mata umarni , Kallon da yakaka take mata kallo ne me kaifi da yake ɗauke da fasasarori da dama ,wanda ta gaza ɗaukar masa fassara guda ,  tana ganin lokacin da ta fisge hannun ta daga cikin na kamal ɗin ta nufi ƙofar da ta ga ya nufa da ita , ba tare da ta sake waiwayowa gare ta ba , A sanyaye ta miƙe cikin ran ta tana harhaɗa kalmomin da zata yi amfani da su wajen kalmaso kan yakaka ta rarrashe ta kamar yadda ta saba yi mata a duk lokacin da tayi mata wani gagarumin laifi , gefe guda tana tunanin ware wani kaso me ɗan tsoka daga cikin kuɗin da kamal ɗin ya bata ta danƙa mata su duk domin su taimaka wajen  shawo kan ta cikin sauki.   Da wannan tunanin ta faɗa motar ta bar gidan tana duban agogon hannun ta da yake nuna ƙarfe tara saura ƴan mintoci , sama ta haskaka da hadarin da yake haɗuwa da ke nuni da koyaushe cikin dare ruwa zai iya sauƙa . Kar ka kuskura ka sake taɓani , Ta ce da shi lokacin da take samun wajen zama bisa kan kujerar gaban tafkeken gadon ɗakin na alfarma .   Wata dariya ya kwashe da ita yayi sufa ya faɗa gadon rubda ciki .    Kai yarinyar nan salon ki na burge ni , wat....    Zan sha BURKUTU , Ya tsinkayi muryar ta ta katse masa kalaman sa , waigowa yayi yana daga kwance ya dube ta , fuskar sa na bayyana mamaki yace : Burkutu ? Eh tace da shi tana tsattsare shi da idanun ta , Ni bana shan giyar gargajiya ,"blue moon ," ita ce giyar da nafi ƙauna , yanzu ma ita na sha ƴar kaɗan , kin san tana da ƙarfi shegiyar giya ce , ko za ki iya sha na zubo miki kaɗan ki taɓa irin ta ? Kawo min ta ce da shi a taikaice . Miƙewa yayi ya fita Yana fita ta miƙe tsaye ta shiga kai kawo a ɗakin tana yarfe hannu , da tayi zaton zata iya , a zaton ta tana da ƙarfin zuciya , ya kome yake shirin kufce mata ? Me zai faru da ita idan har shirin ta bai tafi dai-dai ba , ??   Jin motsin taɓa ƙofar ya sa tayi saurin komawa ta zauna , Ya shigo hannun sa ɗaya riƙe da kwalbar giyar blue moon ɗaya kuma kofin gilashi da ya zubo ƴar ƙanƙara a ciki , Zuba giyar yayi ƴar madaidaiciya ya miƙa mata ,   Idanun ta na duba ƙasa ta ce da shi ka fara sha , Jim yayi riƙe da kofin sai kuma ya kai bakin sa ya ɗan kurɓa , Ya Sake miƙa mata , Ka cika min taf Tace da shi ba tare da ta bari sun haɗa ido ba , Keeeee hahaha , wannan fa blue moon ce ba'a mata haɗama yanzu nan za ki ji ki warwas kin gaza motsi, ba ta wasa bace wannan , ke kin san kuɗin ta kuwa ? Yafi jarin baban ki . Bana shan wannan , warin ta bai min daɗi ba ka kawo min wata idan akwai , nafi son wacce zata ƙara min kuzari ,   Ɓata rai yayi !  ya tsaya kallon ta  sai kuma ya kwashe da wata dariyar sakarci , Tunda ta ƙara kuzari kike nema bari na kawo miki Amstel kina shanta yau ji za kiyi kamar an miki allurar da ake yiwa dawakai ,    Ya ƙarasa zancen yana kafa kai ya sha fiye da rabin wacce ya zuba a kofin ya ajiye sauran ya fita yana gama hanya tare da jaan wani siririn fito irin na wanda duniya ta yiwa daɗi . Yana fita ta miƙe tare da murɗa ƙofar ta fito , ɗan yawatawa tayi da idanun ta cikin daƙiƙoƙi ta fahimci ɗaukewar ƙafar da ya ƙaru a wajen domin mutum ɗaya ta hango a zaune ya tasa kwalaban giya a gaban sa , Da sassarfar da take harɗe kafafun ta ta taka tana nufar ƙofar ficewa daga wajen bakin ta ɗauke da addu'o'i iri-iri ,    Siit ji mana , ? Numfashin ta ya nemi siƙewa da jin muryar wani yana dakatar da ita , bata juya ba sai ma ƙaimi da ta ƙara ba tare da ta bari ta ƙarasa jikin ƙofar ba ta miƙe hannuwan ta duk biyu ta tura ƙofar , ta jefa ƙafar ta waje . Tana jin sa yana sake sanar da ita ba fa nan kamal ɗin yake ba , Ba ta saurare shi ba , ta kara da saurin da yafi kusa da gudu tana keta farfajiyar gidan ta nufi ƙofar da suka shigo gidan , Ƴar ƙaramar kofar da take maƙale da babbar ƙofar gidan ta nufa kai tsaye ta tura ta , cikin sa'a ƙofar ta buɗu da gudun gaske ta ƙarasa ficewa daga gidan , Tsawa tare da rugugin hadari da ya karaɗe sararin sama bai toshe mata kunne daga barin jin tashin muryar kamal ba , hakan ya sa a diririce ta tura ƙaramar ƙofar gidan da yake daura da ita ta faɗa , Ga babbar sa'ar ta babu kowa a harabar ɗan madaidaicin gidan me tsari , dan haka cikin sauri ta cire hijabin ta daga cikin jakar ta ta zira akan kayan ta , ta sake zaro niƙabin ta ta fara ƙoƙarin ɗaurawa , Gurnanin da ta ji daga gefen ta kaɗan shi yasa zuciyar ta dokawa da ƙarfi , tare da taimakon hasken ƙwan lantarkin ta waiga da sauri idanun ta suka shiga cikin na wani ƙosasshen kare da yake kwance daga gefe kusa da ita , Ɓurɓushin tsoron daga ƙasan ran ta ya fara toroƙo kafin baki ɗayan jikin ta ya ɗauki rawa , Cikin abunda yake gaza da minti guda ta juya da gudun gaske ta fita a gidan tana banko ƙofar , karen kuwa bai jinkirta ba ya rufa mata baya da ƙaƙƙarfan haushin sa , suka zuba ƴar tsare akan titin da yake shal babu kowa saboda dare da ya fara yi ƙarfe goma saura , haɗi da garin da yake gangame da hadari . Gudu take tamkar wacce aka ɗaurawa tayoyi a ƙafa , bata san gabas ba bare yamma , karen wanda haushin sa ya jawo ƴan uwan sa karnai na bakin titi suka zama su uku , su ma bin ta suke da iyakar gudun su . Ruwan saman da ya tsinke kamar da bakin ƙwarya shi ya sake gigita yakaka ,  har numfashin ta na barazanar ɗaukewa duhu na fara mamaye ganin ta . Hakan shi ya hana ta fahimci karnukan sun koma baya sun daina bin ta tunda ruwan saman ya fara sauƙa . Duk da cewa dare ne kuma titin babu kowa , amma shi ka'idar tukin sa ne haka baya cika gudu , sannu-sannu yake tuƙin sa cikin nutsuwa ƙira'ar Sheik Sudais cikin Suratul Al-Araf  tana tashi ta cikin sifiƙun motar , fitowar sa kenan daga asibiti inda ya yini yana wasu muhimman aiyuka ( shigar da bayanai akan marasa lafiyan da yake ɗauke da alhakin duba su )  saboda hutu da yake son rubutawa na sati shidda ya je gida ya gaida iyayen sa , sannan yayi amfani da damar wajen sasantan tsakanin iyayen sa , lokaci yayi da yakamata ace an kawo ƙarshen koma menene ya jawo rabuwar ta su tsawon waɗannan shekarun , ga su suna zaune babu abokan rayuwa wanda hakan ko kusa ba martabar su bane , duba da cewa shekarun su sun fara jaa , À son ransa a maida auren iyayen nasu kafin bikin Rahima wanda za'a yi a farkon sabuwar shekara me kamawa nan da watanni bakwai masu zuwa , Bai yi aune ba ta ɓullo daga kwanar gaban sa da gudun gaske ,  da ba domin a hankali yake tafiyar ba da babu abunda zai hana ya yi ciki da ita da mota. Da ƙarfin gaske ya jaa burki ganin yadda ta bugu da jikin motar ta sa , ruwan saman bai hana shi ɓalle murfin motar ya fito ba , ya zagayo da sauri ta sashin da take dai-dai lokacin da ta miƙe tsaye daga faɗuwar da tayi , Da gudun ta tayi bayan sa ta ɓuya bayan ta riƙe jikin rigar sa ƙam da dukkanin hannuwan ta biyu , jikin ta ko'ina rawa yake . Tsai yayi yana jin yadda wani nisasshen yanayi a wani shuɗaɗɗen lokaci makamancin wannan yana bijiro masa , KARE , KARNUKA su na bina dan Allah ka taimaka min , zasu kashe ni . Muryar ta tayi amsa kuwwa a kunnuwan sa ta tafi ta tado ƴar uwar ta da take binne cikin ran sa me ɗauke da salo da kalmomi iri ɗaya da suka fito a jere cikin yanayi me kama sak da wannan , dan haka sai ya jiyo baki ɗayan sa yana fuskantar ta bayan ya fizge jikin sa , Hasken walkiya da na fitilun gefen hanya sun gaza wajen fiddo masa da ainahin kamannin fuskar ta da take rufe da niƙabi illa idanun ta da suka jirkita da zallar tsoro , da ya gaza jurar kallon su . A hankali ya janye ganin sa daga kan ta ya dubi gefen titi inda ta ɓullo , ko alamun karnai babu , dan haka ya juya da sassarfa yana nufar ƙofar motar sa , cikin ran sa yana aiyanawa wannan wani sabon salo ne na matan banza . Ki koma gida dare yayi . Yace da ita . Halin ruɗanin da take ciki bai isa jirkita mata tunanin da zai sa ta gaza gane shi ba , zuban ruwan sama akan kamilallar fuskar sa ba zai taimaka ba wajen hana ta shaida kamannin sa duk kuwa da rabuwa da yin tozali da tayi da shi na tsawon wasu shekaru , shi ɗin ne dai mutumin da Allah yake kawo mata shi a duk lokacin da take tsaka da neman agaji me girma a cikin rayuwarta , Wani irin yanayi ta tsinci kan ta a ciki me nawi , da ya sanya ta sauƙe ganin ta ƙasa , A hankali ya tada motar sa ya gifta ta tana me cigaba da tsayuwa a wajen ruwan sama na sauƙa kan ta cikin yanayi na rashin madafa , Tsaki yayi a karo na biyu lokacin da yake sake kai ganin sa jikin ɗan madubin saman motar sa yana hango ta , cikin nutsuwa ya murɗa kan motar sa ya taka ta yayi baya tare da dawowa inda ya bar ta , Shigo na kai ki gida . yace ga ita ba tare da ya dubi sashin da take tsaye ba . A hankali ta buɗe gidan baya na motar ta shiga ta rufe ƙofar tare da takurewa da jikin murfin motar tayi ƙasa da idanunta , wata irin kunya da nawin sa take ji ., girman laifin ta ninƙaya yake cikin tunanin ta yana ƙara girmama a idanun ta , zuciyar ta na raɗa mata ai ita ɗin bata cancanta da sake samun wani taimako kome ƙanƙantar sa daga gare sa ba . ko motsi ta gaza yi , gani take cikin duk wani motsi da zata yi zai iya gane ta , zai fahimci ko ita wacece , da zuwa yanzu ta tabbatar bai shaida ta ba . me zai faru idan ya gane ta ? Wataƙila ya wurgata kan titi . Tana son tace wani abu ko da kalmomi biyu ne , ina Falmata ?  A wanne hali take ciki ? A sama ta tsinkayi muryar sa , Wacce unguwa kike Muryar ta a dushe ƙasan maƙoshin ta ta sanar da shi , Babu wanda ya sake magana a tsakanin su har zuwa lokacin da suka kawo unguwar , ƙofar gidan malama maryam ta nemi ya dakata zata sauƙa , baice ƙala ba ya tsayar da motar , Na-nagode ta furta tana barin motar kai tsaye ta isa jikin ƙofar gidan malama maryam ta shiga ƙwanƙwasawa sannu kan hankali . Jaan motar sa yayi yana barin unguwar lokacin da zuciyar sa ke nace masa wajen son bijiro masa da tunanin waccen tana haɗa su da yanayin wannan , amma bai bari tunanin yayi tasiri ba ya kunna karatun Al'qur'ani yana cigaba da saurara . bai son tuno wani abu da ya shafe ta , ita ɗin ai bata cancanta da kutsowa cikin tunanin sa ba ko kaɗan  . A hankali ta zame ta zauna a jikin ƙofar bayan shuɗewar ƙugin tayoyin motar sa bisa kan kwalta, ruwan saman na cigaba da sauƙa a jikin ta , kukan da take riƙewa tun shigarta motar ta saki da ƙarfi , kukan ha'incin da samy baby ta yi mata , kukan nadamar kuskuren da ta aikata a rayuwar ta, babu abunda take so a dai-dai lokacin irin ta buɗi ido ta ga falmata da mama a tare da ita , ta haƙiƙance sune kaɗai jinin ta a duniya sune baza su taɓa cutar da ita ba , Takurewa tayi a wajen tana karkarwar sanyin iskar ɗaukewar ruwan sama da yake busa ta . Washegari Samy baby tana tsakiyar baccin ta na tofon gira misalin ƙarfe goma na safe ta tsinkayo bugun ƙofar gidan ta tamkar a tsakiyar kan ta , Mummunan tsaki ta jaa , bayan ta miƙe tana haɗa maballan gaban rigar baccin ta , kan ta ko ɗan kwali babu ta fito , dai-dai lokacin da aka kaiwa ƙofar wani mugun bugu tamkar za'a ɓalla ta , Kai wai wanne ɗan^ yake ƙoƙarin ɓalla min kofa , tamkar na ci bashin sa ban biya ba ? Ta furta hakan a tsawace  tana ƙoƙarin zare sakatar ƙofar , bata gama zarewa ba ta ji anyi ciki da ita da ƙofar , tayi baya taga-taga ƙiris ya rage ta faɗi , A fusace ta ɗago kan ta hannun ta dafe da goshin ta , da ƙofar ta buga Kutumelesi ,.... Kar ki yadda ki zage ni tsohuwar ƴar damfara , kuɗaɗena na zo ki mayar min da su account , saboda ƙaramar ƴar iskar da kuka haɗa baki kuka damfare ni tun daren jiya ta gudu , dan haka ko naira ɗaya ban yadda a samu giɓin su ba a cikin kuɗina ki dawo min da su yanzu-yanzu . Wani irin fargaba ne ya dirarwa Samy baby , me Kamal yake cewa ? Yakaka ta gudu ? Da kƴar ta tattaro guntuwar nutsuwar ta , Ta juƴa ta fara taku tana cigaba da murza goshin ta ,   Kamal ka shigo muyi magana a ciki , zancen ba na tsaye bane , Ke duba Samira ba inda zan shiga kawai kuɗaɗen nan zaki dawo min da su domin ko hannun ta bata yadda na taɓa ba tayi tafiyar ta tun jiya , bayan wahalar neman ta da ta saka ni cikin ruwan sama ƴar^ ke daman kin san yarinyar nan wata gara ce irin haka har zaki karɓi kuɗina akan ta ? Yi sauri dallah ki dawo min da su , da akwai inda zan tafi daga nan bani da lokacin ɓatawa . Kallon ba yadda zan yi Samy baby take bin Kamal da shi , ta fahimci a bugen sa yake tatil kamar koyaushe , idan har ta nemi yin gardama kan zancen kuɗin nan kome zai iya faruwa da ita ,   Bani account number Ta ce masa tana shigewa ɗaki ɗauko wayar ta , daga ƙasan ran ta take jin mummunan ɓacin rai na taso mata akan abunda Yakaka tayi mata , ashe rashin mutumcin Yaks har ya kai haka ? Ta gudu ta jawo mata irin wannan babbar asara ? Allah ya so bata riga ta kacan-chala kuɗin nan ba da yanzu yaya zata yi da tijarar Kamal ? Tabɗi dole ne ta ɗau mataki akan Yaks , ta nuna mata kuskuren ta saboda gaba kar ta sake gwada mata irin wannan mugun wasan . Cikin mintoci biyar Samy baby ta ɗibga asarar Naira miliyan biyun da suke mallakinta daga jiya zuwa yau , har gumi ne ke tsattsafo mata ,  lokacin da ta koma falo ta zauna bayan tafiyar Kamal da bai bar gidan ba sai da miliyan ɗin sa biyu ta koma account ɗin sa . Ina Yakaka ta kwana ? Shine tambayar da Samy baby take yiwa kanta , Zumbur ! ta miƙe tsaye lokacin da ta ayyana inda Yakaka ta kwana , gidan Malama Maryam . Ɗan siririn mayafinta da yake ajiye a falon shi ta ɗauka ta yafa akan rigar baccin jikin ta , ta fito a fusace bayan ta rufe ƙofar gidan da makulli ta zagaya layin bayan su kai tsaye ta doshi gidan malama Maryam da tunda take sau ɗaya ta taɓa taka gidan , Sai fa yau da zata kuma zuwa . Ko sallama bata yi ba ta danna kai cikin gidan , ilai kuwa tana shiga falon ta tadda Yakaka tana zaune ta jingina da jikin ɗaya daga cikin kujerun falon da farantin cin abinci a gaban ta wanda bata kai ga sa hannun cikin sa ba . Da shigowar ta Yakaka ta miƙe da alamun firgici a fuskar ta wacce ta ɗan kumbura kaɗan tayi jaa , Anty Samy .. Da hannu ta dakatar da ita , ki min shiru Yaks , ashe baki da mutumci haka daman? Ƙyat ! tayi Kwafa ki wuce mu tafi gida inason yin magana da ke . Malama Maryam wacce tashin muryar Samy baby ya sanyata fitowa daga cikin ɗakin ta , ta ƙaraso wajen tana bin Samy baby da kallon nazari Yayar Yakaka lafiya dai ko ? Anan Yakaka ta kwana tun jiya cikin dare take ta kuka taƙi sanar da mu abunda ya sameta , dan Allah idan laifi tayi miki kiyi haƙuri ki yafe mata Wani kallon banza Samy baby ta jefawa Malama Maryam saboda ta fara fahimtar duk wani taurin kai da take hango alamun Yakaka zata gwada mata har da taimakon koyarwar Malama Maryam wacce ta lura duk wasu sabbin ɗabi'un Yakaka daga gurin ta ta kwafe .    Ki wuce mu tafi   Ta sake maimaitawa tana mayar da duban ta kan Yakakar Da wani irin yanayi cikin muryar Yakaka , wanda yake fallasa halin baƙin cikin da zuciyar ta ke ciki , tace    Bazan bi ki ba Anty Samira ni daga nan Maiduguri zan koma wajen Falmata da ƴa ta , bazan taɓa yadda nayi yadda kike so nayi ba . BAZAN SAKE YIN ZINA BA    Kif-kifta ido Samy baby tayi tamkar bata ji da kyau ba ,ta karkata kai tare da ɗage shi sama ta ce : Kika ce me Yaks ? Bata jira ta amsa mata ba ta ɗora da cewa .   Maiduguri ?? Sai ta kwashe da wata gajerar dariya , Wa kika sani a Maidugurin ? Waye naki a can wa kike da shi a duniya ? Da sauri Yakaka ta amsa mata har muryar ta na sarƙewa Ƙanwata Falmata da ƴata Mama ! Hahaha ! Yaks kenan ai Falmata da ƴar jaririyar da kika gudu kika bari duk sun riga sun mutu , au ashe ban faɗa miki ba ko ? Sorry lokacin kina tsaka da jarabawa ne kin san fa ke mayyar karatu ce ... Kukan kurar da Yakaka tayi ta tura samy baby ta faɗa kan kujerar bayan ta , ta hau ɗare-ɗare kan ta , tare da maƙure mata wuya shi ya hana samy baby cigaba da zancen da ta shiryo shi a yanzu ,    Me na miki Anty Samira ? Me na miki ? Ƙarya kike min koyaushe Ƙarya kike min baki taɓa faɗa min gaskiya ba Ƙarya kike Falmata na bata mutu ba , Ƙarya kike yi bata mutu ba  , ki faɗa min gaskiya me kike shiryawa game da rayuwata ? Me na miki ? Da taimakon Malama Maryam suka ɗaga Yakaka daga kan Samy baby wacce duk Yakaka ta yakushewa wuya , gabaɗaya ta birkice musu kamar me tashin Aljanu , ihu kawai take tana cewa Falmata bata mutu ba ƙarya ne ,    Addu'o'i Malama Maryam take tofa mata tana riƙe da ita , Bata cikin hankalinta ta ɗago kan ta hawaye wani na korar wani a fuskar ta , Ummi , ki kaini Maiduguri yanzu-yanzu dan Allah , ki kaini naga Falmata Zan kai ki Yakaka ki nutsu ki daina wannan ihun babu kyau , kiyi innalillahi wa inna ilahi raji'oon , kiyi addu'a ki bar kukan nan haka . Gƴaɗa kai take ba domin tana fahimtar kalmomin Malama Maryam ba , bakin ta ya gaza furta kalma guda illa karkarwa da laɓɓan ta ke yi , zuciyar ta ke wani irin bugu da tsananin tsoron da yake barazanar tarwatsa mata zuciya , kalmar Mutuwa ga Falmata tayi mata tsauri da girma ta yadda zuciyar ta gaza ɗauka , tunanin ta ya guntule cikin rashin sanin takamaimai a halin da take ciki ,  ƙiyayyar samy baby sabuwa fil take yaɗo cikin ran ta . Da baya-da-baya Samy baby ta ƙarasa barin falon tana jin yadda tsoron halin da ta ga Yakaka a ciki na cika mata zuciya ,    Niamey Niger Cikin makonni uku da ƴan kwanaki visa Falmata da Mama ta fito  , Biyamuradi Youssouf bai jinkirta ba wajen fara shirye-shiryen tafiyar su , bayan ya ɗauki hutun sa na kwanaki talatin a wajen aikin sa , tare da gudurtawa cikin ran sa idan kwanakin sun gaza wajen yin abunda ya kai su , zai dawo ya rubuta takardar neman iznin hutu batare da biyansa albashi ba ya koma . Cikin satin zuwan sa Maradi sau biyu , bayani sosai ya tsarawa Maimartaba tare da hajiya Umma kan cewa aiki ne zai kai shi zouwa ƙasar Amurka , Babu shakku cikin ran su suka masa addu'o'in samun nasara kan abunda za shi nema , tare da fatan dawowa lafiya . Bangaren matan sa ma bai samu matsala da Siyama ba , wacce take da tsananin yarda ga mijinta , dan haka ta hau shirya masa ƴan kayan cimaka da zai iya yin guzurin su zuwa ƙasar da za shi , zuciyar ta cike taf da kewar sa da ta fara tundaga yanzu , lokaci-lokaci tana sharar ƙwalla rabuwa da masoyi duk da cewa ba sabon abu bane shafe kwanaki masu yawa irin haka basu tare , amma haka kawai taji wannan tafiyar tasa ta tsaya mata a zuci ko domin ƙasar zai bari bakiɗaya zuwa wata nahiyar ? Ga Gimbiya Maimounatou kuwa sam bata gamsu ba da zancen barin sa ƙasar , hasalima batun tafiyar sa ya kawo mata tsaiko ne kan wani Al'amari da take ɗorarwa akan sa , sai take ganin tamkar da gayya ya tsiri tafiyar ,hakan ba kome bane face salo ne na kauda-bara da ya sha faruwa a duk lokacin da take kan gaɓa na son cimma ƙudirin ta , sai dai baza ta fasa ba , ba kuma zata gaza ba wajen cigaba da bibiyar kome a sannu har sai haƙar ta ta cimma ruwa . Dan haka babu ƙarsashi a tare da ita suka yi bankwana bayan ta haɗa masa ƴan nata kayan cimakan da basu cika yawa ba saboda zuciyar ta da take shaƙare da takaici , duk da cewa tayi iyakar ƙoƙari kamar yadda ta saba ta boye abunda ke binne ƙarƙashin ran ta . Daga Tafeeda kaɗai ya so samun tangarɗa wanda yake da sani sosai akan harkar aikin su , ya kuma titsiye Biyamuradin da tambayoyi akan aikin da yace zai kai shi US , sai dai ga mamakin sa hanya-hanya da zamiya iri-iri Biyamuradi ya dunga yi masa da ya hana shi sanin takamaimai gaskiyar lamari game da tafiyar ta shi ,  karshe dai ya fahimci babu shakka akwai abu me girma da Aminin sa ke ɓoye ma sa wanda kuma lalle wannan abun ya shafi rayuwar sa ta kurkusa , sai ya ɗiga ayar tambayar . Cikin ran sa ya ƙudurci bin diddigin kome . Duk wani shirin tafiyar su ya kammala , kamar yadda Biyamuradi ya Alƙwarta ga Hajja , ya ƙira direban da zai kai ta ana washegarin ranar tafiyar su , ya sanar da shi gobe da safe ya zo su kama hanyar Nigeria da Hajja  . Jakar matafiya karama da Babba Ya kawo musu , Ya miƙa Babbar ga Hajja , yana cewa Hajja ga wannan jakar ki shirya suturun ki ciki , wannan ƙaramar kouma na Fatima ne , kayan ta kaɗan zata ɗauka ba wasou masou yawa ba kawai aboubouwa masu muhimmanci da zata iya bouƙata su zata zouba a ciki, ita kouwa Mama ba sai an ɗauka mata wasu suturu ba , kaya biyu kawai sun isar mata idan munka kai can duk za'a saya wasu suturu sabouda yanayin mu da nasou ba ɗaya bane . Au Babban soja wai da ni har mun shirya kayan a cikin manyan akwatuna ? Fiye da rabin kayan nasu ma ai mun loda su a akwatuna har huɗu , ashe tafiyar ba ta guzurin kaya bace ikon Allah . Ɗan murmushi yayi , a ah hajja a ajiye waɗannan suturu a gida zamu sayi wasu a can . To ai babu kome , huta-roro ( waken gizo ya ƙi 'Ya'ya )  wannan babu neman masu dakon kaya a tashar jirgin sama , oh duniya kullum cigaba ake watau ita turai ba'a zuwa da kayayyaki dayawa ?  Dayake ma can gidan kaya ne , kamfaninnika ne da su na suturu sai ka zaɓa ka darje , kuma fa irin atamfofin nan namu arhar bulus ne da su a can ko Babban soja  ? Cikin gundura da hirar hajja , yace hajja ai can basou sanya tufafi hakka irin namou , su suturun su duk kananun kaya ne sai kouma kayan sanyi , Firfito da idanu tayi bayan ta rafka tagumi fuskar ta cike da alhini ta ɗora da : Ƙananun kaya ni hauw'u ? Da kai da Falmatar watau duk ƙananun kaya za ku dunga sawa ? O'o ana bariki a turai , to ita dai Mama ku dunga suturtata da kyau saboda yanayin lafiyar ta daman ba kumari ta cika ba . Kai tir da rayuwa da ba ta Musulunci ba Sai kuma ta ɗan saki murmushi tunowa da tayi da wani abu , Kuma ka ga ƙananan kayan zasu amshi jikin ku Babban soja , musamman ma ita Falmata , ƴar riga da wondon nan na zamani ka daure ka saya mata ɗanɗasa-ɗanɗasa ba ƙaramin haska ta zasu yi ba .   Ɗan zunkuɗawa yayi akan kujerar jin an taɓo masa inda yake masa ƙaiƙayi ,   Hajja ina Fatima tare da mama sun ka tafi tun shigowata ban ji motsin su ba , Nan suka shiga gidan su Zainaba ta je ayi mata kitso da kunshin tafiya . Ai tana gaf da shigowa ma . Ƙunshi kuma hajja ?    Tafiyar mu ai ta neman lafiya ce hajja ba'a buƙatar duk irin wannan shirye-shiryen , Ta gefen ido hajja ta dube shi , Babban soja ai shi ƙunshi ado ne ga ɗiya mace ... Sallamar Falmata ita ta hana ta ƙarasa zancen , Da gudu mama ta saki hannun Falmata da take yiwa jagora ta nufi Baban ta   Papa bienvenue , ta ƙarasa shigewa jikin sa da ya buɗe mata hannunwan sa , ta kwantar da kan ta a ƙirjin sa , ya shafi kan ta yana sauƙe idanun sa akan Falmata da take ƙarasowa wajen jikin ta sanye da dogon hijabin ta har ƙwauri ta zauna daga ƙasa a gefe , Sashin da take hasashen yana wajen ta fuskan ta cikin nutsuwa ta gaishe shi fuskar ta kadaran-kadahan . Ya amsa yana bin fuskar ta da kallo da kitson da aka mata ya sake fiddo ƙyallin fatar ta tare da bayyana hasken goshin ta , Hajja wacce bata zama a tsakanin su ta yunƙura ta miƙe riƙe da jakankunan a hannu ta nufi ɗaki , tana ƙiran mama wacce tayi biris da ita taƙi amsawa sai ma sake lafewa da tayi a jikin baban ta . Fatima ya shiri ? Kin kammala kou ? Eh mun kammala tace To madallah gobe insha Allah zamou tafi ku zama cikin shiri kin ji kou ? Toh ta amsa tana gyaɗa kai ! Shiru ne ya ɗan gitta tsakani , kafin mama ta ɗago kan ta daga jikin Baban ta , Papa , an mana kitso ni da Mamaa na ka gani yayi chau ? Ta janye hular kan ta , manyan kitson chuku da aka mata suka bayyana , duk da kitson manya-manya ne amma sun yi kyaun zane kasantuwar ta me yalwar gashi sai ya ƙarawa kyaun kitson armashi . Shafa kan nata yayi yana murmushi yace , wow c'est très beau ,    Da dariya ta bar jikin sa ta nufi Falmata tana zuwa ta fara kici-kicin buɗe mata kai , Mamaa ke ma ki nunawa papa kitson ki , yafi nawa ma chau ko papa ? A hankali ya gyaɗa mata kai yana jingina bayan sa da jikin kujerar ba tare da ya janye ganin sa daga kan su ba ,   Ture hannun ta Falmata tayi ta ɗan ɗaga sauti ,    Ki bari mama ba na hana ki buɗe min kai ba ?    Ba tare da ta sauke hannuwan ta daga kan falmata ba tace   Ai papa ne zai gani . Tsawa tayi mata lokacin da take son ta sauƙe mata hijabin a tilas , Firgita tayi ta ja baya ta rakuɓe tana ƙwalan-ƙwalan da ido tare da raba kallon ta tsakanin mamar ta da baban ta ,     A hankali wasu siraran ƙwalla suka silalo daga gurbin idanun ta ganin an mata abunda ba'a saba yi mata ba ba kuma tare da an rarrashe ta ba , Cikin ran ta taji shirun da tayi tare da sanin manufar sa ,  dagulewar zuciyar ta ya zo dai-dai da zubar hawayen Mama  , Hannu ta ɗaga ta fara lalubar inda take jin tashin shisshiƙar kukan ta , ta jawo ta jikin ta tare da ɗaura ta akan cinyoyin ta ,   Kwantar da kan ta tayi da ƙarfi a jikin mamar ta gami da fashewa da kukan da tayi tanadin sa , Kamar ruwan maɗaci haka take jin ɗacin sautin kukan ta daga cikin zuciyar ta, dan haka ta fara aikin lallashin ta , Hannu ta kai ta zame hajibin nata , ƙananan kitson da aka mata yir-yir suka bayyana   Ta karya murya cikin kuikoyon muryar mama tace : Papa ka ga kitso na yayi chau ?? A hankali ta ɗago kan ta daga jikin ta idanun ta jage-jage da hawayen rikici , ta washe ƴan haƙoran ta lokacin da take kama dogon jelar kitson shade ,'( me hawa biyu ) da aka tufke shi ya sauƙa kan dokin wuyan ta , ta waiga tana duban Baban ta wanda duk abunda suke yana bin su da ido , ransa cike taf da ƙauna tare da shauƙin soyayyar dake tsakanin uwa da ɗiyar ta . Muryar ta kamar ba ita ke kuka yanzu ba tace , Papa ka ga kitson mamaa na yayi chau ko ? Yunƙurawa yayi ya matso sosai gaban kujerar da yake kai , Yana ƴar dariyar yadda fuskar falmata take a ɗaure tana wani takurewa yace , Ai tayi nissa daga can bani ganin kitson nata , ta matso nan kussa na gani kou ?  Ya ƙarasa zancen yana karya wuya . Eh Mamaa ki zo ya gani , Ta jawo hannun Falmata , gudun rikici ya sa Falmata ta biye mata ta taso ta biyo ta , gaf da ƙafafun sa Mama ta zaunar da ita ,    Idanun sa ya sauƙe akan kitson da suke yir-yir kamar inji ne ya jera , ƙwarai kyaun kitson ya birge shi . Basu yi aune ba ta jaa hannun Baban ta ta ɗora akan Falmata , Papa ka ga ni ? Ta ce tana washe masa haƙoranta . Kasa janye hannun nasa yayi daga kan ta , saboda wani irin yanayi da yake ji yana zagaya illahirin jikin sa , Tundaga kan yatsar kafar ta taji tashin tsikar jikin ta , da wani yanayi da ya tsinka gudun jinin jikin ta , irin yadda bata taɓa ji ba a rayuwar ta , bakiɗayan jikin ta babu kuzari , Ganin shirun su ya tsawaita ya sa Mama ta raba ganin ta a tsakanin su , kafin ta ɗan turo baki , Papaa , baka ce kitson mama yayi kyau ba ?? Cikin dai-daita nutsuwar sa ya janye hannun sa daga kan ta ya janyo Mama Zuwa jikin sa , Kitson Maman Mama yayi kyau sossai très belle . Batare da ta ƙara daƙiƙa guda ba ta miƙe , tana nufar hanyar ɗakin hajja , zuciyar ta na cigaba da tsananta bugu , cikin kowanne takun ƙafafunta take jin idanun sa na yi mata rakiya . 9:30pm Falmata ta sake muskuɗawa tana rufe bakin ta daga gajerar hamma da take yi akai-akai saboda bacci da ya fara cin ƙarfin ta , Ita bata kaiwa dare sosai take yin bacci a yawancin lokuta ƙarfe takwas da rabi na dare sun yi bacci ita da Mama , shiyasa yau da hajja ta buƙaci son suyi magana ta zo kuma ta tadda ta tana shafa'i da wutiri , bayan ta idar kuma ta ɗora da addu'o'i , duk sai zaman jiran ya gundure ta bacci yake kawo mata samame , Falmata , Falmata . Ko kin yi baccin ne ? Na'am hajja idona biyu . To taso ki zo nan kusa da ni magana nake so muyi , a hankali ta taso ta taho inda take jin tashin muryar hajja ta zauna daga gefen ta bisa dardumar sallah . Fatima ki nutsu da kyau ki saurareni , da kunnen basira , kin ga wannan tafiyar da za kuyi ke da Mijinki tamkar wata babbar dama ce Allah ya baki da za kiyi ƙoƙari ki dai-daita zaman ku ke da shi , ki ƙarbo martabar ki ta ɗiya mace , cikakkiyar matar aure , ke yanzu ba yarinya ƙanƙanuwa bace ba , da za'a zauna ana yi miki bayani dalla-dallah baƙi da fari akan aure , shekaru biyar ana cikin na shida da yin auren ku , lokaci yayi da yakamata ku kawo ƙarshen wannan zaman kai da ƙafar da kuke yi a tsakanin ku , ku haɗa kai ku rungumi junan ku cikin inuwa da alfarma irin ta aure , Ke kece mace bance ba ki bada kan ki ba , amma ki yunƙura kiyi hoɓɓasa cikin dabarun ki na ɗiya mace da Allah yayi miki baiwa da su ,  ki karkato da hankalin mijinki kan ki , tunda jajayen sawun ki , da sauran damar ki , kina kuma tare da makaman yaƙin da zasu taya ki karɓo kambun ki tun kafin damar ki ta kufce miki , futsanci , jin kai , halin ko inkula da miji ba naki bane , yanzu anwuce wannan zamanin , zamani ne muke ciki na tarairayar miji a gatata shi ta yadda za'a masa riƙon tsauri da kufcewa zata masa wahala , kin dai ji na faɗa miki . turai zaku je , kiyi ƙoƙari ki sau jiki , ki shige masa , ƴan kananun kayan nan da yace ana saka su a can ki sa ya kawo miki su dayawa kullum ki dunga yi masa ado da su , daman ga ki da kyakkyawan jiki..... Ƙananun kaya fa kika ce hajja ? Falmata ta katse ta tana yamutsa fuska . Eh su nace to meye ba mijinki bane ? Wani ma yayi rawa bare ɗan makaɗi ? Cewa nake kowa a garin su yake sawa ? To ke meye laifin ki idan kin yiwa mijinki ado da su ? Ji min rashin wayo . Ta mula kafin ta cigaba da cewa : Ƴar rangwaɗa da kisisina irin ta mata dunga yi masa , ki raba kan ki da ƙwalafacin Mama ki fara tunanin hanyoyin da za ki bi ki faranta ran mijinki saboda kin ga dai dai-dai gawargado shi yana nuna miki kulawa ke kece kike ƙin bada haɗin kai , to ki sake zane tun dundumin ki da danshi , shi mijin mace huɗu ne . Ga ƴan magunguna nan na karɓo miki su musamman a wajen uwar zainaba , ta tabbatar min da ingancin su su ma zasu taimaka miki ƙwarai da aniya . Anya hajja idanun nawa kuwa magungunan nan zasu min aiki ? Amma dai ba na sawa a ido bane kin san fa a asibiti sun hana ni zuba magani a ido , Mts' ana raba ki da kiwon awaki kina kyalla ta haihu , wanne maganin ido kuma ?? Wannan maganin gyara tsakanin ku ne ke da mijinki , idan kika daure da shan su suma zasu taka rawar gani wajen karkato miki da hankalin sa . Ni zan dunga sha ko shi ? Nifa  bangane bafa hajja . Yo ina kuwa zaki gane ana nuna miki gabas kina bauɗewa yamma , kina girma kina sake shiga daji ., maganin mata ne . Maganin mata ? Ta maimaita da sigar tambayar Eh hajja ta amsa tana dangwara mata kullin maganin a hannu , Karɓi ki sa a cikin akwatin tafiyar taku , da madarar ruwa ko ta gari ake shan su , Taɓe baki falmata tayi , Tana ciro Envelop daga hijabin ta , Hajja ga hotunan Mama din an karɓo ɗazu Baban ta ya bata ta kawo min, Karɓar envelop ɗin tayi ta zaro ƴan madai-daitan hotunan Mama da aka ɗauketa kwanaki uku da suka wuce da zummar hajja zata tafi da su Maiduguri ta kaiwa mutanen gida su ganta domin rabon su da ganin hoton ta tun tana ƴar shekaru biyu , Kai ɗanɗashi hotuna kuwa sun yi kyau kamar a ƙirata ta amsa tar-tar da su , ƴar wayayyar fuskar nan ta fito ,  ai kin ga hakan yafi a tafi musu da hoton ta su ganta ko dan yadda Rahima da Alhaji suke begen ganin ta . Murmushi tayi , jin daɗin Hajja ta yabi 'yarta Hajja kar ki manta dan Allah da saƙon gaisuwata , ga Baba , Yaya dakta , Rahima , kai kowa da kowa dai hajja , ki miƙa musu gaisuwata tare da fatan alkhairi . Insha Allah kuwa duk zasu ji Falmata , kin dai ji duk abubuwan da na faɗa miki ko ? Eh duk naji Hajja , To ki dai yi amfani da cewa ta , idan Allah ya yarda za ki ga amfanin sa . To Hajja . Ƴar dariya Hajja tayi,  to Allah shi sa idan kun dawo nayi farin ganin gamdakatar da sabon ango ko kuwa sabuwar ƙawa . Falmata ta yunƙura ta miƙe tsaye , tana cewa Aina kenan Hajja ? Ko daga can za'a kawo miki ɗan turawa ? kai kai kai Hajja baki da dama . Saƙare Hajja tayi bakinta buɗe , sai kuma ta gallawa Falmata harara . Kinci gidan ku da sauyawa zancena launi , ƴar nema ai nasan sarai kina fahimta ta da gangan kike bauɗewa , oho ni dai na faɗa miki kowa rai yayiwa daɗi ai bayan me shi ne . tana ƴar dariya ta ƙarasa barin ɗakin , kalaman Hajja na kutsawa cikin tunaninta tana ɗora su a mizanin nazari . Washegari Da farar safiya direban da zai kai Hajja Nigeria ya iso , daman da shirin ta tsaf , dan haka babu wani jinkiri aka fito da kayanta aka sanya su cikin mota , Tare da rakiyar Biyamuradi , Falmata da Mama suka ƙaraso jikin motar sallamar bankwana suka yi , Hajja ta shige mota direba ya tada motar suka miƙa hanya Mama tana ɗaga mata hannu . Allah ya kiyaye hanya Hajja ta Falmata ta furta a sarari tana jin yadda kewar ta ke fara kamata , "sabo tirken wawa ', Muje cikki Fatima kafin zouwar le chauffeur mu tahi I'aéroport . Hannun ta cikin na Mama wacce take ta zuba surutu suka juya zuwa cikin gida , kai tsaye ɗaki ta shige ta zauna a bakin gado , tunaninnika suka yi mata dirar mikiya , kewar ahalinta na kassara duk wani karsashi nata , shekaru biyar ɗin basu zo mata da sauƙi ba , ba kuma sun rageta da kome ba wajen jin ƙauna tare da muradin sake ganin wani jinin ta a duniya bayan Mama , duk kuwa da cewa ita ɗin ta kasance daga cikin jajirtattun mutane masu yaƙi da damuwar su, tare da danneta su binne ƙarƙashin ran su , su yunƙura wajen gina rayuwar su a yadda ta zo musu , ba domin ƙarfin zuciyarta ba da tuni damuwar halin da ta tsinci kanta ciki sun kaita ƙasa . A hankali irin nata akwai hangen wani ƙalubale da take yi wanda take hasashen zai iya ɓullowa cikin rayuwar su ita da Mama , daga dangin Biyamuradi , wanda har kawo yau da Mama tayi shekaru a duniya da yake dai-dai da shekarun auren su babu wani dangi nasa ɗaya da ya taɓa zuwa wajen su , ya gan su .  Shi kaɗai suka sani , duk kuwa da yana ikirarin cewa yana da iyaye da danginsa makusanta , to ina suke ? Meyasa basu taɓa zuwa inda suke ba ko su su ziyarce su ? Shin menene aboye wanda su basu kai ga sani ba ? Tsakanin ƙarya da gaskiya wa ake yiwa wasan ƴar ɓoye a tsakanin su da dangin sa ?  Tabbas akwai lauje cikin naɗi . Sai dai koma menene a shirye take tsaf da taryar sa , zata yi kome domin ta bada kariya ga Mama , ƙuɗirinta bazai taɓa sauyawa ba muddin tana numfashi ita zata cigaba da kasancewa garkuwa ga Mama . Ya jima yana tsaye daga dokin ƙofar yana duban ta , a tsawon zaman su da shi da ita koyaushe yanayi ɗaya yake hangowa a fuskar ta idan bata san da wanzuwar sa ba a guri , "damuwa" tana da damuwa wanda yake danganta damuwar ta ta da kansa . Yana sane da cewa shi da ƴar sa sunyi kutse tare da yin karan-tsaye cikin rayuwar ta , ba kuma tare da suna amfanar mata da kome ba . Anya yana yi mata Adalci ?? Gyaran murya yayi da ya sa tayi firgit! Tana gyara zaman hijabin kanta , Fatima tasso le chauffeur ya zou . Jakar kayan su uku babbar ƴan kayan cimaka ne a cikin su da sauran ƙananan tarkacen matafiya , ƙananan biyun suturun su ne a ciki . A shirye suke tsaf , Falmata tana sanye da doguwar riga ruwan sararin samaniya me ɗan nawi ta ɗaura mayafin rigar akan ta ( tayi ɗankwali da shi )  da ɗan madaidaicin hijabin ta , takalman kafafun ta marasa tudu sun shiga da hijabin ta kalar ruwan hoda me haske ( baby pink ) Mama anshirya ta cikin ƴar riga iya guiwar ta da dogon wondo kanta rufe da hular saƙa me nawi mahaɗin safar ƙafar ta dake sanye da rufaffun takalman yara . Biyamuradi ya riƙo hannunta da shima yake shirye cikin shigar kwat da wando ( suit ) ruwan ƙasa , ita kuma ta riƙe ƴan ƴatsun Falmata , sun sanyata a tsakiyar su suka fito farfajiyar gidan , Biyamuradi ya kulle ƙofofin gidan bayan ya kashe duk wasu na'urori masu amfani da lantarki . tazarar ba wata me yawa bace tsakanin su da farfajiyar tashin jiragen sama na ƙasa-da-ƙasa ( Diori Hamani International Airport ) Dan haka cikin ƙanƙanin lokaci suka isa , bayan Bayan bin duk wasu tsare-taren da ya kamata matafiya masu tsallakawa ƙasashen ƙetere suyi tare da zaman jiran dai-daituwar jirgi da ya ɗauke su tsawon awanni uku da rabi , Biyamuradi Youssouf tare da Falmata da Mama suka bi sawun takwarorin su masu tafiya zuwa United States of America , a sawu na farko suka taka matakala ,  kafaɗar sa ta dama ɗauke da Mama wacce ta sarƙafo hannayen ta a jikin wuyan sa , ɗaya hannun nasa  ya zare daga cikin na Falmata da tunda suka shigo airport ɗin yake kaffa-kaffa da ita yana riƙe da hannun ta , duk kuwa da yadda take yawan mutsu-mutsu da hannun tana son zamewa amma ya ƙi kulawa bare ya bata dama , ya maida hannun sa bisa ƙugunta tare da matso da ita jikin sa , a hankali yace da ita , Fatima ki kulla da kyau ki saurari takun ƙafa ta bissa matakala muke , ba tare da ta amsa ba ta gyaɗa kanta , tana jin yadda tsikar jikin ta ke miƙewa . Cikin jerun kujerun first class suka yi mazauni akan kujerun su masu ɗauke da numbobin su da suke fuskantar juna , sai ɗan teburi a tsakanin su , bayan zaman su ya yunƙura tare da ɗaurawa Falmata seatbelt ɗin ta ya koma ya zauna tare da ɗaurawa Mama nata , bai tsimaya ba ya ɗaura nasa . A hankali ya kai hannun sa ya kamo hannun Falmata da yake kan teburin gaban su , ya damƙe hannunta guda cikin nasa dai-dai lokacin da zazzaƙar muryar shugabar masu dauke da alhakin kula da walwalar mutanen cikin jirgin "Chief flight Attendant ," ta karaɗe cikin jirgin ɗauke da sanarwa da take cewa :   “Ladies and gentlemen, this is Rose jackson and I’m your chief flight attendant. On behalf of Captain Mike Abraham and the entire crew, welcome Turkish Airlines flight  non-stop service from Niamey Niger Republic to Washington DC United States of America. Our flight time will be of  9hours and 11minutes. We will be flying at an altitude of  feet/meters 5612 miles . At this time, make sure your seat backs and tray tables are in their full upright position and that your seat belt is correctly fastened. Also, your portable electronic devices must be set to ‘airplane’ mode until an announcement is made upon arrival. Thank you.” Ta sake maimaitawa cikin yaren faransanci . ( Mesdames et messieurs, voici Rose Jackson et moi, votre agent de bord. Au nom du capitaine Mike Abraham et de l'ensemble de l'équipage, accueillez le vol sans escale de Turkish Airlines entre Niamey Niger Republic et Washington DC, États-Unis d'Amérique. Notre temps de vol sera de 9 heures et 11 minutes. Nous volerons à une altitude de 5612 milles. À ce stade, assurez-vous que vos dossiers de siège et vos plateaux sont dans leur position verticale maximale et que votre ceinture de sécurité est correctement bouclée. De plus, vos appareils électroniques portables doivent être en mode "avion" jusqu'à ce qu'une annonce soit faite à l'arrivée. Je vous remercie.") Girgizan da jirgin ya ɗauka shi yasa ba shiri Falmata ta sake ɗora ɗayan hannun ta akan na Youssouf tana ƙanƙame sa  hannayen su suka cure guri guda , kamar yadda zuciyoyin kowannen su ke ƙoƙarin jawo kusanci a tsakani . Idanun sa a kafe kan fuskar ta dake bayyana tsoro ɓaro-ɓaro . Cikin ikon Allah jirgin ya samu dai-daituwa a sararin subahana ya shilla da gudun gaske cikin tafiyar gaibu bisa iska a tsakanin sama da ƙasa . Nigeria Tafiyar kwana ɗaya da yini biyu ta sada Hajja da birnin Maiduguri , da la'asar sakaliya motar da ta kawota ta dakata a ƙofar gidan Prof . Kai tsaye ta sauƙa ta shiga gidan , tarɓa ta musamman ita da direban suka samu daga sabbin ƴan aikin gidan guda biyu tare da Rahima da daman duk ansan da zuwan su . Bayan magarib ta nemi iznin zuwa gaishe da prof da  zuwan su a ɗazu suka tadda shi tare da baƙi , hakan ya sa basu samu ganin sa ba sai yanzu . Bayan doguwar gaisuwa tare da godiyar da akayi musayar su tsakanin  Prof da Hajja , taƙaitatciyar hira suka yi wanda duk rabin ta akan Al'amuran da suka shafi taɓarɓarewar tsaro ne tsakanin Niger ɗin da Nigeria da har kawo yau Ƴan tawayen Boko Haram basu saduda sun bar yin kisan mimmiƙe tare da ɓarnannaki tsakanin ƙanana da ma manyan garuruwan Niger da Nigeria ba . Sannan kuma har kawo yau gwamanatin ƙasar Nigeria ta gagara kawo ƙarshen hare-haren ƴan kungiyar duk kuwa da cewa cikin ƙasar tushe da MAFARIN kafuwar ƙungiyar da ta jefa Dubunnan rayukan Al'umma cikin HARGITSIN RAYUWA yake . Shin yaushe ne kome zai kawo ƙarshe ? Yaushe ne abubuwa zasu koma dai-dai ? Yaushe ne za'a ƙira ƙungiyar Boko Haram da shuɗaɗɗan lamari da ya zama tarihi ?  Allah Shine Mafi sani . Hajja ta miƙe ta ƙarasa gaban Prof tana miƙa masa envelop ɗin dake ɗauke da hoton Mama , Alhaji ga hoton Amaryar taka ta Niger ka ga yadda ta girma duk da ƙarancin lafiyar ta amma ta miƙe . Miƙa hannu yayi ya karɓa yana dariya , dai-dai da shigowar Doctor Hamza wanda ya dawo daga Masallaci . To toh Masha Allah , Babu kome ai kowacce cuta Allah yayi maganinta , sai dai idan har sanin ɗan Adam bai kai ga gano maganin ba . Ƙwarai maganar ka dutse Alhaji .     Cewar Hajja . ya zaro hoton yana gyara zaman gilashin idanun sa , bayan sun haɗa baki wajen amsa sallamar Doctor Hamza , ka ga Babban Likita , Likita bokan turai , ƙarshen ƙwaƙƙwafi da bincike sai likita , lalle tafiyata bana me sa'a ce tunda naci karo da kai , shekaru fiye da biyar rabona da na ganka . Murmushi yayi yana zama daga gefen ƙafafun Prof . Hajja sannun ki da zuwa , da fatan kin  samu isowa lafiya ? Lafiya ƙalau Likita ,yaya bayan rabuwa ? Ya iyalin naka ? Duk kowa lafiya hajja . To Alhamdulillah . Masha Allah wannan Amarya tawa ai tafi kama da ƴaƴan nasara , ga dukkanin Alamu tana da wayo . Prof ya furta haka yana mayar da hotunan cikin envelop ɗin . Wayo kuwa na sosai Alhaji ai Mama sai godiyar Allah ba shakka tana da kaifin ƙwaƙwalwa da saurin ɗaukar abu Allah shi rayata , ya bata lafiya , yayi Albarka cikin rayuwarta ita da sauran yaran musulmai baki ɗaya ! Ameen Ameen Alhaji Hajja ta amsa tana sanya hannuwanta biyu ta karɓi envelop ɗin da yake maida mata , ta miƙe tana yi musu bankwana tare da barin falon ta koma cikin gida . Baba , wacce yarinya ce hajja ta kawo maka hoton ta ? Doctor Hamza ya tambayi Prof . Ya buɗe baki da zummar bashi amsa shigowar ɗaya daga cikin dattijan unguwar da suke cin abincin dare tare da Prof ya katse musu hirar . Abuja Yakaka ce a zaune kan hannun kujerar falon Malama Maryam gabanta kuwa babbar jakar kaya ce da take shaƙare taf da kaya , daga gefen ƙafafunta ma wata ƴar matsakaiciyar jakar ce . tana shirye tsaf cikin dogon hijabinta da yake har kusa da idon sawun ta , fuskar ta fayau babu ko kwalli , ramar da tayi ta fito sosai akan fuskar ta da idanunta da suka ɗan zurma ciki . daga gefe a cikin falon Lubna ce a zaune tayi jugum tana kallon Yakaka wacce idanun ta ke kallon ƙasa , tayi shiru tamkar ba sune masu yin dararraki ba muddin suna waje guda . Malama Maryam ce ta fito itama shirye take , ta kai dubanta ga Yakaka tana jin yadda tausayin ta ke sake narkar da ranta tabbas Yakaka tana buƙatar majiɓanci cikin Rayuwar ta . Yakaka tashi mu tafi , lubna taya ta ɗauko kayan ku kai cikin mota Abban ku yana jiran mu , kar mu rasa motar farko ko ta biyu , saboda mu samu isa da wuri tafiya daga Abuja zuwa Maiduguri da tazara gara muyi sammako .  Jikin Lubna babu kuzari ta miƙe tana gyara zaman hijabin jikinta ta sunkuya ta ɗau ƙaramar jakar tare da kama gefen babbar ta taya Yakaka riƙewa , Sun zo tsakar gida Lubna ta jaa ta tsaya da hakan ya sa Yakaka waigowa . idanunta cike taf da ƙwalla tace Sahiba irin rabuwar da zamuyi kenan babu bankwana ? Shekaru biyar ba kwana biyar bane Sahiba ban so ba zaki tafi tare da maɗaukakiyar damuwa . ɗan guntun murmushi Yakaka tayi , Sahiba kin san har abada kina cikin mutanen da bazan iya mantawa da su ba cikin rayuwata , cikin kowanne irin hali na tsinci kaina , nima zanyi kewar ki Lubna , ta ƙarasa zancen siririyar ƙwallar da bata shirya zubowar ta ba na sauƙa bisa ƙuncin ta . Idan kika tafi a yanzu waye zata maye min gurbin ki ? Waye zata zama babbar ƙawata a bikina ? Da ke muka tsara kome Yakaka . Idan Allah ya yarda zan dawo Lubna , zan halarci bikin ki na ɗau Alƙawari , amma dole na tafi a yau shekaru biyar Falmata tayi cikin rashina , Hon ɗin da aka matsa da ƙarfi shi yasa suka fara taku cikin hanzari ba tare da sun sake musayar wata kalma ba a tsakanin su . Ƙarfe takwas da rabi na safe motar da su Yakaka tare da Malama Maryam suka shiga domin tafiya Maiduguri ta ɗau hanya ɗoɗar . Tafiya ce me nisa ta tsawon fiye da awanni takwas tsakanin Babban birnin tarayya Abuja da Birnin Maiduguri dan haka a saboda yawan tsaye-tsaye akan hanya daga jami'an kula da hanya da suke gudanar da bincike , ya sa dare ya fara shiga har ƙarfe shida na yammaci ta gota , wanda hakan kuma ya sa dole su yada zango a garin Damaturu saboda lokacin dokar hana zirga-zirgan motoci ya shiga ( curfew)  ala tilas suka kwana a tasha , Washegari da hantsi ƙarfe tara suka shiga garin Maiduguri , a idanun Yakaka babu wani sauyi da garin ya samu tsawon shekaru biyar ɗin ko kuwa dan hankalinta bashi kan duban yanayin garin ne ? Baki ɗaya ta ƙagauta ta ɗora idanunta akan ƙanwarta da ƴar ta . Tsawon lokacin rabuwar ta da garin bai sa ta manta da sunan unguwar da ta bar Falmata ba , dan haka bayan sauƙar su a tasha kai tsaye ta shaidawa direban taxi da ya ɗaukesu da kayan su unguwar da zai kai su . tafiyar mintoci 15 kachal ta sada su da unguwar , layi bayan layi ta kwatantawa direban har zuwa gaban gidan da a koyaushe yake yawan samun gyaran da yake sake fiddo kyaun tsarin ginin dai-dai da na zamani . Bayan sun sauƙe kayan su a gefen hanya daga jikin katangar gidan Yakaka tace ga Malama Maryam Ummi bari na shiga na nema mana iznin shiga da kayan mu . To Yakaka . taku ta fara yi tana jin yadda zuciyarta ke bugu da fargabar da ta rasa takamaimai dalilin samuwarta daga ƙasan ran ta , ta kawo kusa da ƙofar gidan aka buɗo Babbar ƙofar ya danno hancin motar sa yana ƙoƙarin fitowa ... !!!! Assalamu Alaikum wa Rahamatullah ta'aala wa barkatuhu . Yan uwa masu karatu Maza da Mata,  ina mika sakon gaisuwa ta tare da fatan Alkhairi a gareku. Sannan ina mika godiya ta ga dukkanin daukacin Mutanen da suka samu damar kirana a waya da wadanda suka bar sakonni su na gaisuwa tare da addu'o'in samun waraka ga 'ya'ya na,  har ma da wadanda Allah bai basu dama ba,  kalmar nagode ai tayi kadan wajen bayyana muku jin dadina , sai dai nace Alherin Allah ya isar muku a duk inda ku ka yi bigire .      Ehen Uhum uhun-hun Kai daga jin wannan guntattakin sautukan da suke tasowa daga kasan maƙoshi ka san da su nake,  o'e da o'e ko kuwa dai a takaice na ce ghost r-r-readers 😂 Ba kome , Ba kuma zance kome ba , amma ku saurari haɗuwar ku da ɗanliti , Ah to meye ? Ai shine zai rama min irin cin tuwo a ƙoƙon da kuke min 😢. A cigaba,  eh nace a cigaba da labewa a bayan labule . 😂 😂 Nagode .    MAFARI ( Hargitsin Rayuwa ) Umm'muaz 35 Doctor hamza ba tare da ya dubi sashin da Yakaka take tsaye ba yayi wucewar sa yana waya da 蓷aya daga cikin abokan aikin sa na nan Asibitin Maiduguri wanda ya masa 茩iran gaugawa sakamakon neman sa da ake a asibitin jahar saboda wani aiki na gaugawa da za'a yiwa wata mata da take halin bu茩atar taimako , Kan ta a 茩asa tana satar kallon gefen fuskar sa , zuciyar ta cike taf da addu'o'i iri-iri , ta wuce ta 茩arasa wajen maigadi wanda ya tattara dukkanin hankalin sa akan ta , Sama-sama ya amsa gaisuwar ta ya 蓷ora da tambayar ta wajen wa ta zo ? Wajen Rahima na zo . tace da shi tana fatan kar ya hana ta shiga gidan saboda wannan maigadin ba茩on fuska ne ba wanda ta sani a da ba ne聽 Kallon tsanaki yayi mata bai hango wani alamun rashin gaskiya a tattare da ita ba , Ki shiga tana ciki . Yace yana komawa kan 蓷an bencin sa na zama . Hamdala tayi bayan ta yi masa godiya ta taka tana nufar cikin gidan da bai zamto ba茩o ba a gareta , tsarin sa bai sauya ba illa zuciyar ta da take cike da taraddadin hasashen da irin fuskar da Mutanen gidan zasu 茩arbe ta da hakan ya hana ta kuzarin isa cikin gidan cikin 茩an茩anin lokaci Da duk takun ta guda kunnuwan ta suke sake kusanto mata tashin muryar ta suke,聽 da bata riga ta manta amonta ba ko dan ita 蓷in tana daga cikin mutanen da suka gwada mata 茩auna a duniyar ta ne ? Hajja dan dai kince kin manta fuskar maman ta ne amma idanunta sak na mamar ta ne , sosai tana 蓷ibar yanayi da mamarta sai dai ko kamannin Baban ta yafi 茩arfi , ai babyn nan 茩arshe ce a kyau wallahi kamar naje Niger na kwato ta nake ji , Allah sarki baby na Allah dai ya baki lafiya , yasa a dace wajen neman maganin nan , Allah kuma ya ji茩an Mamar ki me kirkin nan . Da murmushi hajja ta amsa da Amin Amin Rahimatu聽 聽聽 A hankali ta sau茩e idanun ta a bayan Rahima lokacin da ta 茩araso 茩ofar falon , wacce ta juya baya tana 茩o茩arin sa茩ala tangamemen hoton Mama cikin jerin hotunan da suke killace a jikin bangon inda aka tanadi sashi na musamman domin ajiyar hotuna , 茒aya daga cikin hotunan da hajja ta zo da su ne da ta kai aka wanke mata shi zuwa Babban takardan hoto aka yi mata gidan sanya hoto na musamman tare da sanya shi a cikin gilashi . Ganin ta ta mika kan hoton , fuskar da ta gani jikin hoton ya sauya bugun zuciyar ta nan take , a hankali take wara idanun ta tamkar wacce ta warke daga makanta , kamar yadda take jin zuciyar ta tana bu蓷ewa da wani irin yanayi 茩a茩茩arfa , 茩ofofin gashin jikinta baki 蓷aya suka bu蓷e suna tsattsafo da gumi聽 , Taku ta fara yi tana 茩ara kusantar hoton da zuciya da tunaninta baki 蓷aya suka tafi ga fuskar dake jikin sa. Ha茩i茩a bata ta蓳a ganin ta ba amma kusancin dake聽 tsakanin uwa , mahaifiya da abunda ta haifa daga cikin jikinta ya wuce wasa ya kuma wuce聽 hankalin duk wani me tunani 茩auna ce me rassa da take ya蓷o a dun茩ule da babu me iya ganin zurfn ta bare a iya hasaso iyakar ta聽 , Bayan Rahima ta zo daf ta tsaya tana sake nutsar da idanun ta akan fuskar mama wacce tayi 拼ar kyakkyawar dariya a hoton. Hajja wacce ta mi茩e tsaye daga gefe tayi sororo tana bin Yakaka da ido kafin tace Ke , Ke , Ke baiwar Allah lafiya kike kuwa ? Zaki shigo mana gida haka sangam-sangam babu sallama bare neman izni ? Kin kuma zo kin yi tsaye 茩ere-re uwa wacce ta ha蓷iyi ta蓳arya ince ko baki da lafiya ne ? Rahima wacce bata ji tsayuwar Yakaka kusa da ita ba , saboda raggon taku marar sauti da Yakaka tayi a yayin isowa wajen , ta 蓷an waiga sashin hajja lokacin da take gama sar茩afe hoton a inda ya dace tare da janye hannun ta daga jikin hoton ta waigo tana cewa Hajja da wa kike magana ne ? Fuskar ta ce ta kusan ha蓷uwa da ta Yakaka da ya sa ta 蓷an jaa baya Bismillahi waye ha... Kalmomin ta ta ha蓷iye mu茩ut , ma茩wallon ma茩ogoron ta ya motsa kamar yadda idanun ta suka firfito da mabayyanin firgici baro-baro a cikin su , 聽 Shekarun da suka raba ha蓷uwar fuskokin su basu yi yawan da zasu sa su mance da kamannin juna ba . Ya-Ya-Yakaka ke-ke kece ?? Rahima ta furta muryar ta tana makyarkyata kamar yadda kwakwalwarta take hautsinewa da kokonto , Yakaka wacce zuciyar ta ta za茩u da son samun tabbaci akan gudan jinin ta , ba tare da ta janye idanun ta daga kan hoton ba ta lalubo hannuwan聽 Rahima ta dam茩o su da 茩arfi , Rahima, Rahima ni ce聽 , 聽 Ta zarce da tambayar ta wannan ,?聽 wannan Mama ce ? 瞥a ta Mama ? 聽聽 Rahima wacce tunanin ta ya gama dun茩uluwa waje guda , ta fisge hannuwan ta da matu茩ar 茩arfi bata tsaya ba ta taka da gudun gaske tana nufar 茩ofa , kafin ta 茩arasa ficewa ta 蓷aga murya tana sanar da Hajja . Hajja ki gudu wallahi Fatalwar Maman Mama ce wannan . Turus hajja tayi tana bin bayan Rahima da kallo , kafin ta sake waigo Yakaka wacce bata bi ta kan kalaman Rahima ba tamkar ma dai bata kai ga fahimtar me kalaman Rahima ke nufi ba . Ta saka hannu ta 蓷ago Hoton ta ciro shi daga mazaunin sa , tare da ri茩e shi da hannuwan ta duk biyu , tamkar ta ri茩e yar jaririyar ta . Kai tsaye ta nufo Hajja da hoton , fuskar ta da wani irin yanayi na chaku蓷uwar tsantsar farinciki da kuma fargaba tace Wannan 拼ata ce ko ? Mama ce ko ? Kafin ta 茩araso hajja ta juya da 拼ar sassarfa tana 蓷ingisa kafafun ta da basu cika lafiya ba , Un-un-un 拼ar nan , ni kuwa ina zan sani ? Mutum dai baya 茩in ta Mutane wai ance da 蓳arawo ya gudu聽 , Bi Rahima can dai kin tambaye ta Dan Allah . Garam ! Hajja ta rufo 茩ofar 蓷akin ta . Sa茩are tayi a tsaye tana son harha蓷a tunanin ta domin ta kai ga fahimtar meyasa ta ga kamar ana gudun ta ? Ashe girman laifin ta har ya kai ya sa ta zama abun gudu a wajen mutane ?聽 Falmata ina Falmata ? Ta san idan kowa zai guje ta a duniya a zare Falmata a cikin su , Falmata baza ta ta蓳a gudun ta ba , ina take ? Ta juyo da nufin fitowa ta nufi sashin Baba , sai ga Rahima tare da wani mutum wanda bata kai ga sanin sa ba . Mallam Kabir ga ta nan , ta nuno Yakaka wacce take tsaye 茩i茩am rungume da hoto . Dan Allah kana ganin ta ? Ina ganin ta mana Hajiya Rahima , ai wannan Mutum ce , ba Fatalwa ba ,聽 hala an samu akasi ne wajen jin wani labari akan ta ? Ke baiwar Allah wacece ke ? Daga ina kike聽 ? Me kuma kika zo yi nan?聽 Zuwa lokacin Yakaka ta fara hasaso abunda yake faruwa , dan haka fuskar ta na bayyana sabon alhini ta matso tana cewa . Rahima ni ce Yakaka , ba Fatalwa ba ce ni , ban mutu ba , waye yace na Mutu ???? Ina Falmata ? Ba tare da Rahima ta ce 茩ala ba , bata kuma yadda ta 茩arasa kusa da Yakaka ba ta sake juyawa da 蓷an gudu ta nufi sashin Baba , da daman daga can 蓷in take shine ma ya ha蓷o ta da Mallam kabir 蓷in da ta zo ta same su tare suna ganawa , Tana cikin yiwa Baba bayanin dawowar Yakaka 拼ar gudun hijira wanda suke da tabbacin mutuwar ta a wajen haihuwa shekaru kusan shidda da suka wuce , Sai ga Mallam kabir tare da Yakaka wacce take biye da shi聽 . Da ido Baba ya bisu bayan ya amsa sallamar su ,聽 har suka 茩araso cikin falon inda Yakaka ta nemi waje daga can gefe guda ta dur茩usa bisa guiwowin ta , Mallam kabir bai zauna ba yayi bankwana da prof tare da juyawa kan takun sa ya bar wajen . Prof bai yiwa kamannin Yakaka sani na sosai ba amma tabbas ya shaida fuskar ta , saboda ya ta蓳a ganin ta a farkon zuwan ta gidan sa , sannan a 蓷an ta茩aitatcen zaman da tayi a gidan tana zuwa gaishe shi lokaci-lokaci . Babu alamun firgici a tare da shi yake amsa gaisuwar Yakaka , wacce kan ta ke a sunkuye . Cikin nutsuwa irin ta manyan mutane da suke da tarin ilmi ya soma da tambayar Yakaka daga ina take ? Me kuma ya faru da ita tsawon shekarun da tayi bata nan ? Bai shigo mata da batun labarin mutuwar ta da yake tabbatacen Al'amari ba a wajen su a tsawon shekarun da tayi bata nan . Tambayoyin sa suka fargar da Yakaka tare da tuno mata da Malama Maryam da ta baro can a layi fiye da mintoci ishirin , Wacce ta san zata taya ta fuskantar mutanen ta da tarin laifukan da suke kan ta , Tare muke da ba茩uwa Baba , a min iznin na shigo da ita . Je ki shigo da ita babu kome . Bata jima ba suka dawo da tare da Malama Maryam wacce聽har ta fara shiga halin damuwa ganin lokaci ya 蓷an jaa batare da ta ga dawowar Yakaka ba . Cikin nutsuwa da kamalar da Allah ya hore mata Malama Maryam ta gaishe da prof , sannan ta gabatar da kan ta a matsayin Malamar Yakaka wacce ta 蓷au darasi a wajen ta tsawon shekaru biyar da 蓷oriyar watanni , a garin Abuja , daga haka ta tsagaita . A hankali muryar Yakaka ta fara tashi tiryan-tiryan take bada labari tun daga irin Gadar zaren da Samy baby ta ha蓷a mata har kawo ranar barin ta Maiduguri da ta sanyata ta tsallake ta bar Jaririyar ta a ranar da ta haife ta , da zummar zata kai ta Abuja wajen mahaifn 拼ar ta suyi aure ta dawo ta 蓷au yar da 茩anwar ta . Wacece ita Matar da kika bi ? Menene聽 dangantar ku da ita ? Tambayar Prof ta katse Yakaka . Shiru Yakaka tayi na 蓷an wani lokaci , tunowa da tayi da irin rufin asirin da Doctor Hamza ya yi mata a farkon kawo ta gidan ya bayyana ta a matsayin 拼ar gudun hijirar da mijinta ya mutu ya bar ta聽da ciki ,聽 茦aramin tunani irin nata tare da mummunar 茩addara suka sa ta sanya 茩afafu ta ham蓳arar da irin tarin rufin asirin da Allah ya yi mata a tun wancen lokacin da hakan ya jawo a yau ita da kanta zata tona binnannen sirrin nata聽 . Domin a yanzu ta 蓷au al茩awarin baza ta sake yin 茩arya ba , dan haka idanun ta na tara 茩wallar nadama da irin laifin da ta aikata ta koma baya , kan ha茩i茩anin gaskiya ta 蓷orar da labarin ta tun daga farkon shigowar su birnin Maiduguri zaman su a sansanin su, da zaman da suka yi聽 a gidan Madam saly , shigowar Biyamuradi rayuwar ta wanda ta ambace shi da "sojan wata 茩asa ," har zuwa zaman ta a Abuja tare da dawowar ta a yau bata boye duk wasu gaskiyar da yakamata ta bayyana su ba ga mutumin da shine na farko da suka samu mafaka mai cike da karamci da tarin 茩auna a 茩ar茩ashin sa , Shiru ne ya gifta na tsawon wasu mintoci , da hakan ya bada dama ga malama Maryam ta 蓷ora da sake bada kyakkyawar shaida ga Yakaka , yadda ta jajirce wajen neman ilmi ha蓷i da yadda ta cije tare da taimakon Allah ta hayewa fa蓷awa ga rayuwar karuwanci kamar yadda ita samy baby ta so da ta aikata . Mamakin mazajen guda biyu shi yafi kome yin tasiri a tunanin Prof, da har ta kai shi ga gaza cewa wani abu . A zahiri yau ta bayyana a gareshi cewa daga 茒an sa Hamza har shi wancen mutumin da ya zo har nan gurin sa ya 茩arbi auren 拼a a wajen sa duk 茩arya suka wanzu tsawon lokaci suna gindaya masa akan rayuwar marayun yaran su biyu . Wanda a zahiri 茩aryar ta su ta cutar matu茩a gaya , ba su kuma kyauta ba . 茦aryar da Hamza yayi ita ta tokare ta hana shi yayi yun茩urin nemo yarinyar ya dawo da ita ta zauna 茩ar茩ashin kulawar sa kamar yadda a tun ranar da ya kar蓳e su ya al茩awartawa kan sa , wanda hakan ba wani abu ne me wahala ba kasantuwar sa babban Mutum , amma sai hamza yayi masa 茩arya cewa ta mutu har ma yayi jana'izar ta a asibiti , wanda a zahiri tun lokacin聽 shi Hamza yana da masaniyar guduwa tayi , ko me yasa yayi hakan oho ! Sai kuma shi wancen mutumin Niger da ya riga ya san irin mummunan ta'asar da ya aikata na lalata tarbiyar yarinyar nan , amma kuma shine ya sake dawowa ya rufe shi a baibai tare da kar蓳e 蓷iyar sa domin sake samun gara蓳asa har aka 茩ara masa da 茩anwar ta a matsayin mata duk a tafarkin 茩arya ?? Wannan wane irin son zuciya ne ? Meyasa ne gaskiya tayi 茩aranci ? Shin 拼an gudun hijara ba 'ya'ya bane ba ? Ba mutane ne masu 拼anci da galihu irin na sauran Al'umma ba ?聽 Da rayuwar su zata zam ba a bakin kome ba ? Za kuma a dunga yin walagigi da su cikin rashin kulawa da tozartawa , a maishe su ba a bakin kome ba , shin za蓳in su ne rabuwa da iyayen su , dangin su , garuruwan su ? Ko kuwa 茩addara makamanciyar wannan bata iya fa蓷awa kan kowa ne ? Idan har ya tabbatar da duk labaran da suka bayyana a gare shi gaskiya ne , babu shakka zai yi tsayuwar daka cikin rayuwar 拼an gudun hijirar nan guda biyu , zai zama katanga tsakanin su da duk masu shirin tozarta su a sannu kuma zai 蓷au hukuncin da ya dace akan Hamza da 蓷an mutan Niger . Muryar Malama Maryam ita ta sanya shi nisawa , ya maida ganin sa kan ta . Baba ayiwa Yakaka hakuri a yafe mata babu shakka tayi laifi tare da zallar wauta amma domin Allah a 蓷au hakan a matsayin kaddara a cigaba da godewa Allah da ya sa har ta dawo gida lafiya ba tare da wani mummunan lamari ya auku gareta ba , Babu kome baiwar Allah mun gode 茩warai Allah ya saka miki da Alheri kan yadda kika kula da ita , kema Allah ya duba miki naki iyali , Allah ya 茩ara mana yawaitar irin ku cikin Al'umma masu taimako domin Allah . Cikin jin da蓷i Malama Maryam ta amsa da Ameen . 瞥ar boyayyar Ajiyar zuciya Yakaka ta sau茩e ganin yadda Alamu ke bayyanuwa yadda take zaton tsanantar lamarin nata duk bai kai haka ba , A hankali ta 蓷ora idanun ta kan Rahima wacce ita ma kallon ta take , suka ha蓷a ido kafin Rahimar tayi mata guntun murmushi marar sauti . A yanzu hankalin ta ya kwanta ta kuma amince Yakaka ce da gaske ba Fatalwa ba聽 . Ita ma ta mayar mata da martanin Murmushin , 茩aunar junan su tamkar a jinin su take , duk da tarin abubuwan 茩i da Rahima ta san yakaka ta aikata su a yanzu , hakan bai sa ta ji kamar ta tsane ta ba . Kalaman Prof ya sa Yakaka sake nutsuwa ta mayar da hankalin ta kan shi , Bisa ga doron kuskuren da kika riga kika aikata su Abubuwa biyu zuwa uku sun faru , Na farko labarin mutuwar ki , a gare mu tuntuni kin mutu tundaga ranar da kika gudu kika bar 'yar ki . Na biyu shine zuwan da mutumin da ya 茩ira kan sa mijin ki uban abunda kika haifa yayi , Na ukun su shine tafiyar sa da yayi da 'yar sa tare da auren 茩anwar ki a lokaci guda da ni da kaina nayi waliccin auren a nan falon nan na bada auren 茩anwar ki Fatima ga mijin ta uban 'yar ki na kuma 蓷anka masa ita suka tafi tare 茩asar su niger tare da rikiyar Hajja me wurya . Da ace Yakaka ta ta蓳a sanin yadda ciwon Ajali yake da babu shakka zata iya cewa shine ya dirar mata a lokacin saboda wani irin abu me kaifi da ta ji ya taso mata daga 茩asan mara ya zo 茩irjin ta ya tokare ta , Muryar ta a shi蓷e ta wufto kalaman da suke kan harshen ta ta watso su ga Prof idanun ta tsaye 茩em a kan fuskar sa Falmata ce tayi aure da Baban Mama ? Da sake tabbatarwa Prof ya amsa mata da Haka kalamaina ke nufi. Abunda take jin ne ya watsu a cikin jikinta ya barbazu tamkar an watsa mata wuta kafin ya sake dun茩ulewa a ma茩ogoran ta ya tsaya , Yaa Allah , Yaa Allah , Allah na tuba kar laifin da na aikata ya shafi Falmata , Allah ka dawo min da Falmata , Allah ka... Mul-mulan hawayen da suka fara 茩waranyowa daga idanun ta tare da fashewar 茩ullutun da yake wuyan ta shi ya hana ta cigaba da magana illa kukan da ta fashe da shi marar 茩arfin sauti , Kuka ne irin na mutumin da ya ke a halin 蓷imuwa tare da nadama kuka ne irin na ba yadda zan yi , kukan neman taimako , Baki 蓷ayan su irin kukan da take ya ta蓳a zukatan su , Musamman Malama Maryam da Rahima , A bangaren Prof duk da cewa ya ji tausayin ta amma ya bar ta da hakan a matsayin sakamakon laifin da ta aikata . A hankali Rahima ta 茩arasa inda take ta sanya hannu ta dafa ta , Kiyi hakuri Yakaka tashi mu shiga cikin gida , ki bar kuka hakan , Mi茩ewa tayi ta fara taku ba tare da ta cewa kowa kome ba ta wuce , Malama Maryam ta rissina ta yiwa Prof sallama tare da shaida masa gobe da sassafe zata kama hanyar komawa gida Godiya ya sake yi mata , suka rabu suna bin juna da kalaman fatan alheri . Bayan fitar su bai jinkirta ba ya 蓷au wayar sa ya nemo lambobin wayar Doctor Hamza , Fitowar sa kenan daga ICU inda ya jonawa marar lafiyar da aka 茩ira shi domin ita wasu na'urai ya kuma sake duba ta sosai kasancewar ya 茩ware sosai wajen gano tare da bada taimako akan cutar da take damun ta na dajin bakin mahaifa , Mutanen da suke 拼an uwa ga marar lafiyar suka taso caa su kusan rai shidda suna tambayar sa yanayin jikin nata聽 , Nan dai ya kwantar musu da hankali tare da sanar musu da insha Allah zasu yi bakin 茩o茩arin su, su kuma su taya su da addu'a ya ratsa su ya wuce , Ya ji lokacin da 蓷aya daga cikin su tace tunda mun ji yanayin da take ciki sai Maman Bulama ta koma gida ta yi girki ta kawo kuma ta ha蓷o wasu kayan da za'a iya bu茩ata , Maa ki mata bayani yadda zata gane sosai dan ke ce kika iya maganar su ta kurame , Da hannu suka yafito wata mata wacce take zaune a 茩asa daga gefe . Da sauri ta taso ta 蓷an russuna daga gefe , Maa tayi mata bayani da hannu cikin maganar kurame , Cikin sauri take gya蓷a kai alamun tana fahimta, Naira 蓷ari biyu ta zaro daga jaka ta mi茩a mata , ta sanya hanu biyu ta kar蓳a , Ta mata alamar cewa ku蓷in mota ne Ita ma ta gya蓷a kai kan cewa ta gane Har ta juya ta sake dawowa , Tayi musu alamar tambaya tana nuna 蓷akin da marar lafiyar ke ciki . Fuskar ta na bayyana Alhini . Amsa maa ta bata da hannu . Ta juya ta kama hanyar barin asibitin , Doctor hamza wanda ya gama amsa wayar prof da yake sanar da shi kan lalle ya zo yana son ganin sa daga zarar ya kammala abunda yake a asibitin , Ya mayar da wayar sa aljihu tare da juyawa da zummar komawa cikin ofishin abokin aikin sa da shi yayi 茩iran sa domin suyi sallama ya kuma gama yi masa bayani akan irin matakin da yakamata a 蓷aura marar lafiya akai zuwa gwaje-gwajen da ya dace ayi mata聽 茦iris ya rage ya ci karo da matar da ta taho tana ta sauri , sannu Hajiya , Yace yana kaucewa yin karon su , a fisge ya dubi fuskar ta lokacin da take gota shi ba tare da ta amsa ban hakurin da yayi mata ba Cak !聽 Ya tsaya , lokacin da kamannin ta suka yi masa yanayi da na wata da ya sani waye ? khaalty Rahima . Juyowa yayi da sauri da son sake ganin fuskar ta sosai , sai dai ta riga tayi nisa sai tashin hijabin ta ya ke iya gani wanda ya cika da iska saboda saurin da take zabgawa . ***** Daga bakin 茩ofar falon Yakaka ta zame ta zauna , tana wani irin kuka ciki-ciki , a halin da take jin zuciyar ta a ciki babu abunda take fata irin kome da ta ji ace a mafarki ne , bacci take yi ta yi wannan mummunan mafarkin , ta gwammaci ace ta bu蓷i ido ta ga kan ta a gidan samy baby , kai ta amince kome ya faru da ita , da dai dawowar ta Maiduguri ta tarar da wannan mummunan labarin da ya kassara duk wani guntun 蓷oki da mararin sake ganin wani nata a duniya , Aure , wai Aure da Falmata da mutumin da ya yaudare ta ya cutar da ita , ya lalata mata rayuwa tare da bar mata ta蓳on da har abada ba zai gogu ba , ? To wai ma ina ya tafi mata da 茩anwar ta ? Kamar ta ji prof yace ya tafi da ita聽 Ina ya kai ta ? Mutumin da ya saba yin manyan 茩arya da yaudara irin haka kome ma zai iya yi , ina suke ? Kai zata iya barin kome ya wuce ya zama ba kome ba amma banda zaman Falmata tare da wannan mayaudarin domin shi 蓷in ai guba ne, dafin sa kuma ya fi na maja-ciki in yai sara . 茒aga sautin kukan ta tayi tunowa da ta yi da miskinancin 茩anwar ta , Wanne irin hali ta kasance a ciki lokacin da labarin mutuwar da aka ce tayi ya riske ta ? Wata茩ila tundaga lokacin bata sake farin-ciki ba , yaya rayuwa ta kasance mata bayan bata nan ? Wanne irin zama take da wannan macucin mayaudarin ? 茩warai ta gaza a wajen聽bada kariya ga Falmata maimakon haka ma ta zama sila na fa蓷awar ta a hatsari , 茩warai hatsari mana aure da mutumin da ba'a kai ga sanin asalin sa na ha茩i茩a ba , A hankali Hajja ta mur蓷a makulli ta fito daga 蓷akin da ta shige " jin tashin muryoyin su Rahima da Malama Maryam da suke faman rarrashin Yakaka , da sautin kukan ta ya kara蓷e falon Oh ni Hauwa'u naga ta kaina ! yanzu ke 'yar nan me ya miki zafi haka a duniyar nan da zaki zo ki fa蓷i a nan shakwa蓳 , kina rusa ihu ya Amaryar da Angon ta ya mutu daren bu蓷an kai ?聽 Ganin babu wanda ya kula ta ya sa ta samu waje ta zauna kan 蓷aya daga cikin kujerun falon , ta cigaba da cewa , Rahimatu , ince ko dai an fitar da Fatalwar ? Kar sai mutum yana 茩ailula ya farka ya gan ta daf da kan sa . Hajja dagaske Yayar Falmata ce ta dawo , Mamar Mama ashe bata mutu ba Hajja ki taya mu Murna , A kaikace ta dube su tana daga inda take zaune , ta gya蓷a kai . Toh , ah lalle kun kaima Barka , 'Yar nan sannu da bayyana , kuma tsawon lokacin nan da kika shafe bakya nan dandi kike ko kuwa Da'awa ?聽 oh duniya me abun mamaki . Malama Maryam da take zaton Hajja 拼ar uwa ce ga su Yakaka jin abunda Hajja tace ya sa tayi saurin amsawa a 茩o茩arin ta na son ganin ta wanke Yakaka tace聽 , Hajiya , Yakaka yarinyar kirki ce tsawon shekarun nan ta yi su ne wajen neman ilmi , bata aikata wasu munanan aiyuka ba . Ah to babu laifi ilmi ai abun so ne abun nema , shiyasa ma wani mawa茩i ya 茩ira jahili da dattijon biri mai 蓷an kwale . 聽 Ita kuwa Falmata ,uwar蓷akina duk biyu ta ha蓷a ga neman ilmi ga bautar ubangiji ,bautar aure , ta zama gizako katafila a gidan Babban soja , Fatima uwar Mama mata a gidan Babban Mutum ,Allah dai ya dawo mana da ku lafiya uwar蓷akina . Chak! Yakaka ta tsayar da kukan ta , ta mi茩e cikin rashin kuzari ta dawo gaban Hajja ta zauna , Dan Allah ki bani labarin Falmata tare da Mama , ki fa蓷a min a wanne hali suke ciki ? Waye yake kula da Falmata a halin Larurar ta ? Kince Falmata ta shiga makaranta ? Ta koyi karatun addini ? Ta 茩asan ido hajja take duban Yakaka , Falmata da Mama suna nan sumul-luwai 茩alau , 茩ar茩ashin kulawar jigon da ya tallafi rayuwar su , sai girma suke yi suna bun茩asa , karatu arabi da boko kullum cikin yin sa suke ,聽 yanzu haka ma yau kwanakin su shidda da tafiya 茩asar Amurka can turai ince ko kina jin sunan 茩asar ? Hawayen dake fuskar ta basu bushe ba ta kamar yadda bata janye rinannun idanun ta daga kan fuskar Hajja ba , tace Falmata bata kasance ba cikin damuwa ? Bata shan wahalar kome , babu me zaluntar ta ko cin zarafin ta ? Bu蓷e baki Hajja tayi da sigar mamaki Ah kinji min ki蓷ifi ? To wa kuwa zai zalince ta tana tare da mijinta adali gamjigo , wacce damuwa zata kasance a ciki bayan yana kyautayin ta tare da kyautatawa , ke 'yar nan raba mu da mugun fata聽 , 茒an karyar da kai Yakaka tayi fuskar ta ta 蓷an washe ka蓷an daga damuwar da take bayyane , Falmata ta girma sosai ko Hajja ? 茒an tsinken tsintsiyar da hajja ta 蓷auka a 茩asa ta kai bakin ta tana sa茩ace hakori , Idan kika ce girma ma ai kin 蓳ata bakin ki , ta cika tayi fam , 蓳ul-蓳ul da ita kamar kazar gidan gona , ta fiki kome-da-kome , 'yar nan hutun gidan miji fa aka ce miki ? 瞥ar ajiyar zuciya Yakaka ta sau茩e tana Mi茩ewa tsaye , kaso biyar cikin 蓷ari na daga halin da ta tsinci kan ta ciki聽 ya sau茩a ,duk da cewa ba茩in-cikin da yayi mata tsaye a rai yana nan bai gusa ba amma jin lafiyar su ya rage mata matsananciyar damuwar da ta tsincin kan ta a ciki dalilin rashin ganin su , Rahima ki ba mu masau茩i ni da Ummi . Ta furta hakan tana 蓷ora ganin ta ga Rahima , To Yakaka Bismillah ku shigo . Da kallo Hajja ta bi su tana nazari , duk da cewa ta ji da蓷in dawowar Yakaka cikin ran ta , amma bata so zuwan nata a dai-dai聽 wannan lokacin聽 ba domin ko kusa Allah ya sani baza ta so rabuwar Falmata da Youssouf ba wanda ita Hajja ta riga ta san ko wanene Youssouf Abdul-azizou Baskore , ta san matsayin sa na Yarima 蓷an sarki da kasancewar sa Babban soja. Ta san abubuwa masu 蓷an yawa akan sa wanda tsawon lokaci ta 蓷auka tana bincike a kan sa sannu-sannu batare da shi kan sa ya sani ba , ta kuma cigaba da taya shi boye ko shi wanene agare su ita da Falmata duk da cewa ita ta sani , abunda take da ya茩ini akan sa shine rana na nan zuwa da zai bayyana kan sa da kan sa . A ganin ta Youssouf yafi dacewa da Falmata , sannan muddin aka raba auren su a wannan ga蓳ar an cutar da Falmata cuta kuwa me tarin yawa duba da yadda ta rungumi Mama ba tare da ta ta蓳a cin moriyar auren ba ko na lokaci guda tsawon shekun tayi ta yi su ne wajen kula da Mama da hidimar ta da jinyar ta , duk kuwa da miskinancin ta , karon farko yakama ta samu tubarrakin da ke cikin aure sannan kuma Yakaka ta kauda kai ta ha茩urewa Falmata Youssouf su cigaba da zaman auren su idan ya so ita ta nemi wani mijin ta aura , Wannan dalilin ya sa Hajja ta 茩udurci niyyar toshe duk wata hanya da Yakaka zata iya bi ta iya raunata auren Falmata duk kuwa da cewa bata hango alamun hakan daga gareta ba domin ko Youssouf 蓷in bata ji ta gwada ambatar sa ba , amma ko ma dai menene dole ta bada kariya ga auren Yarima Youssouf da Musa茩a Falmata. Washington DC Sau茩ar tsakar dare jirgin su ya yi a Harabar tashi da sau茩ar jiragen sama na 茩asa-da-茩asa dake Washington DC, ( Ronald Reagan Washington National Airport ) Muryar chief flight attendant da ta zagaya cikin jirgin shi ya tada Falmata daga baccin da ya 蓷an dauke ta , Good evening Ladies and gentlemen we have landed at DCA airport in Washington DC, where the local time is 2 :30 and the temperature is 6掳. We hope you have enjoyed your flight with Turkish Airlines this evening and wish you a very safe journey to your final destination . Bonsoir Mesdames et Messieurs, nous avons atterri 脿 l'a茅roport DCA de Washington DC, o霉 l'heure locale est de 2h30 et la temp茅rature de 6 掳. Nous esp茅rons que vous avez appr茅ci茅 votre vol avec Turkish Airlines ce soir et nous vous souhaitons un voyage tr猫s s没r jusqu'脿 votre destination finale . matsanancin sanyin da ya ratsa 茩asusuwan Falmata lokacin da suke tako matakalar jirgin a yayin fitowa da bata ta蓳a jin makamancin sa ba , shi ya sa ta sake shigewa cikin jikin youssouf da yake 蓷auke da Mama bisa kafa蓷ar sa wacce take baccin ta na蓷e cikin nannauyan bargo . Sake kusantata da jikin sa yayi , yana gyara kwanciyar Mama , ya ce 聽 聽 聽聽 il fait extr锚mement froid ( yanayin da akwai tsananin sanyi )聽 Bayan sun bi duk tsare-tsaren da yake dole a yi su a airport yayin da aka shiga 茩asar Amurka a farko, kama daga kan yin hoton yatsu zuwa hoton fuska da sauran su , zuwa lokacin da jakankunan su suka zo hannun su聽 Youssouf ya 蓷au Babbar jakar kayan su ba domin ya so ba ya dan茩awa Falmata 茦ananun jakankunan guda biyu a hannun ta da basu wani cika nawi ba, 拼ar tafiya ka蓷an suka yi suka samu wajen zama a cikin airport 蓷in, Cikin sauri ya bu蓷e jakar kayan sa bayan ya 蓷ora mama a kan 茩afafun sa wacce ta farka tana ta kalle-kallen ba茩on gurin da haske ya wadata shi tamkar tsakar rana. Babbar rigar sanyin sa ya zaro daga ciki jakar shi doguwa ce har 茩auri mai bu蓷a蓷蓷an gaba da turawan 茩asar Amurka ke 茩iran ta ( tribal oversized Cardigan sweater聽 ) Fatima sa rigar sanyi , kadda hunturu shi yi miki lahani , Ya furta hakan lokacin da ya zagaya mata rigar da jikin ta ya taya ta sawa , hijabin kan ta ya gyara mata , ya zarce da riko hannuwanta biyu da suka 蓷au sanyi , ya ha蓷a tafukan su waje 蓷aya , bayan ya kusanci jikin ta sosai , Tsananin sanyin ya yi mata yawa da ya sa take jin sa har cikin cikin ta , jikin ta sai karkarwar yake ,聽 idanun ta da basu cika lafiya ba suka fara tara ruwan hawaye , Lura da hakan da youssouf yayi ya sanya shi rankwafo da kan sa saitin kunnuwan ta , Fatima na bi蓷o miki , caf茅 kafin zouwan notre prochain vol ? ( kafin zuwan jirgin mu na gaba ? ) Muryar ta na 蓷an karkarwa tace Har yanzu zamu sake tafiya wani waje ? Akwai sanyi dayawa anan , bana son sanyi ina da cutar wahalar numfashi . Je sais Fatima que vous allez passer 脿 notre destination finale d'ici 1 heure , ( Na sani Fatima zamu tafi zuwa matsayar mu nan da awa guda ) Shiru tayi ta sunkui da kai . Hannun sa ya kai ya 茩arasa jawo ta jikin sa , ya ha蓷a su ita da Mama wacce ita ma sanyin wajen ya fara damun ta duk kuwa da lodin kayan sanyin da suke na蓷e da jikin ta ya rungume su , Cusa fuskar ta da sanyin yake shiga ta 茩ofofin hancin ta tayi a jikin sa , 蓷umin jikin sa ya sa ta ji sau茩in sanyin tare da yin lamo bata ko 茩wa茩茩waran motsi . Zaman mintoci Arba'in da biyar suka yi , lokacin da sanarwa ta kara蓷e illahirin wajen , Would all passengers traveling to Rochester,聽 on flight FR3522 please have your Passport ready for boarding flight FR3522 now boarding at gate 21, Your flight is ready to Leave. Fatima , tashi mou tafi , notre vol est pr锚t 脿 partir ( jirgin mu ya fara shirin tashi ) . 聽 ***** Tafiyar awa guda da mintuna ishirin a sararin sama ya sada su da birnin Rochester dake babban garin New York 蓷in Amurka da sanyin Asubahi , Bai zauna ba sai da ya yi waya a Hajiya聽 umma ya sanar da ita sau茩ar sa lafiya , tayi masa fatan alheri , suka ajiye waya bayan ya bi蓷i da ta isar da sakon sau茩ar sa lafiya da gaisuwa ga Maimartaba . Yayi Niyyar 茩iran matan sa sai kuma ya fasa , da nufin sai sun cimma masau茩in su sannan . Basu sha wani wahalan zaman jira ba suka sadu da Mr Brian 茩ar茩ashin hukumar asibitin Mayo da Biyamuradi ya riga ya tura musu duk wasu bayanai da ya kamata su sani game da hanyar tafiyar su tun daga Niger har zuwa saduwar su da Asibitin Mayo , Cikin mutuntawa bayan gaisuwar barka da zuwa Mr Brian yayi musu jagora zuwa wajen motar sa da zai ja su kai tsaye zuwa Asibitin su , A gajiye li茩is Falmata tayi mazauni a bayan motar hannun ta cikin na Youssouf , bayan ta zauna ,聽 ta kwantar da Mama a jikin ta da ita ma tayi laushi tu蓳us , bakin nan tsit sai narai-narai da ido take, duk walwalar ta tayi 茩asa . Awanni uku na gudun mota suka sada su da Mayo Clinic , asibitin da yayi suna a fa蓷in 茩asar Amurka da ma聽 duniya baki 蓷aya wajen 茩wararrun likitocin da suka shafi manyan gagararrun cututtuka ha蓷i da ingantattun kayan aiki irin na zamani . Doctor Williams Robert Shine 茩wararren likitan cutukan da suka shafi jini na yara da hukumar asibitin ta dan茩a masa alhakin kula da lafiyar Safiyyah Youssouf Baskore . Dan haka kai tsaye ofishin sa Mr Brian ya dangana da su , babu jinkiri suka samu iznin ganawa da shi da daman ya san da zuwan su . Bayan sun yi ta茩aitatciyar gaisuwa da harshen turancin Amurka cikin sakin fuska Doctor Williams ya nemi da su ma茩ala ( pilot in-ear / Ambasador,聽 ) 拼ar na'urar da ake ma茩alawa a kunne domin amfani da ita wajen fassara yare kai tsaye zuwa kunnen me sauraro cikin harshen da ya fi fahimta . Tarin tambayoyi ne daki-daki ya dunga jero su game da matakan lafiyar Mama , Youssouf na amsa masa , lokaci zuwa lokaci yana auna Mama da na'urorin auna marasa lafiya聽 , Da hakan ya 蓷auke su fiye da awanni biyu , har sai da Mama ta fara 拼an 茩ananun rikici na gajiya , tana ture hannun Doctor Williams daga jikin ta fuskar ta a kwa蓳e . Bayan ya tattara bayanan cikin na'ura mai 茩wa茩walwa dake gaban sa kan teburi , Ya musu iznin tafiya masau茩in su su huta zuwa gobe da zai sake ganin su , Wanda ya kawo su shi ya yi musu jagora zuwa masau茩in nasu da bashi da nisa sosai da cikin asibitin tafiyar mintoci basu wuce goma ba a mota , a tafiyar 茩afa zai kai mintoci ishirin da 蓷oriya , Tun gabannin zuwan su da kwanaki biyar youssouf ya samu nasarar kama hayar 蓷an madai-daicin gida na tsawon watanni hu蓷u a Lofts Apartment, dake 1st St SW. Bakin wata 拼ar 茩aramar 茩ofa ya dakata da su , bayan youssouf ya sau茩e musu jakankunan su da ke bayan motar , Mr Brian ya mi茩e masa 拼an mukullin gidan tare da shaida masa daga yanzu shi aikin sa ya 茩are idan suna bu茩atar wani taimako akwai ma'aika na musamman da zasu zo wa蓷anda aikin su ne kulawa da su da lura da masau茩in su . Bayan tafiyar Mr Brian , Youssouf ya kama hannu Falmata da Mama suka 茩arasa gaban 拼ar 茩aramat 茩ofar gidan tare da sanya 蓷an makulli ya bu蓷e . Sai da ya zaunar da su a cikin falo sannan ya fita ya shigo musu da kayan su cikin sauri-sauri saboda tsananin sanyin da ke akwai duk kuwa da cewa rana ta take tsaka misalin sha biyu na rana agogon can . 茒an madai-daicin falon ya bi da kallo wanda yake tsare tsaf babu wasu tarkace illa kujeru da 拼an tebura sai Tv da kayan kallo daga gefe , tare da kan Tarho ajiye bisa 蓷an teburi聽 , ko'ina a share a goge tamkar da 蓷ai ba'a ta蓳a rayuwa a gidan ba . Idanun sa ne suka sau茩a akan Fireplace ( 蓷an wajen da ake tanada domin hura wutar 蓷umama 蓷aki ) da sauri ya 茩arasa wajen cikin zuciyar sa yana hamdala , ya harha蓷a 拼an kututturan itatuwan ( ironwood ) da ya tarar a wajen da basu cika yawa ba , ya 蓷au poker tare da cinna wuta a jikin itatuwan聽 , Hannun ta ya ri茩o ya kawo ta gaban wutar ya ajiye ta ya 蓷au mama ya 蓷ora bisa cinyar sa , suka yi shiru suna聽 拼an kara hannuwan su 蓷umin wutar na ratsa su , suna jin yadda jijiyoyin jikin su ke warwarewa , jinin jikin su na gudana . Fatima muyi sallah sai na fita ga wajen gari na bi蓷蓷o mana kayan cimaka da amfanin gida , To , Ta amsa tana mi茩ewa ri茩e da hannun Mama Hannun ta ya ri茩o suka shiga 蓷aya daga cikin 蓷akunan biyu da suke manne da juna , 蓷an madaidaicin gado ne聽 a 蓷akin na kwanciyar mutum biyu da yake shimfi蓷e da rigar katifa sai matasan kai biyu, gefe kwabar kaya ce , 蓷an 茩aramin agogo bisa teburin gefen gado shine abu na 茩arshe da yake girke cikin 蓷akin Gaba ka蓷an daga fuskar gadon ban蓷aki ne wanda ake iya hango kome dake cikin sa ( mai murfin gilashi ) da a turance ake kiran sa da ( Framless Glass shower Door ) Tare suka shiga ban蓷akin ya gwada mata wajen alwala . Bi yayi ya dudduba tsarin gidan da bashi da girma sai tsaruwa 蓷an cas da shi kamar a 蓷auke , bayan 蓷akuna biyun da suke falon akwai kitchen da ke 蓷auke da 拼an abubuwan bu茩ata da ya zama dole a kitchen , cikin kitchen 蓷in anyi killatatcen guri domin cin abinci , Sai 茩aramin laundry dake 蓷auke da na'urar wanke kaya . Daga haka babu kome a gidan sai fa shinfi蓷a蓷蓷en Hardwood floor ruwan zuma da ya malale ko wanne lungu da sa茩o na gidan . 茒aya 蓷akin ya shiga wanda ya tarar da shi ya 蓷ara wancen a girma haka ma kayan ciki sun fi na wancen girma sannan a cikin sa akwai 蓷an 茩aramin fireplace da babu a 蓷ayan 蓷akin , Cikin sauri ya shiga ban蓷aki domin yin uzurin sa , abunda ya ba shi mamaki tare da yi masa da蓷i a lokaci guda bai wuce ganin Falmata da ta gama 蓷aura Alwala tar a gaban shi ba tamkar suna ban蓷akin tare , nan ya fahimci ban蓷akin 蓷aya ne me 茩ofa biyu a tsakanin 蓷akuna biyu da ake 茩iran irin sa da ( jack and jill bathroom )聽 sai dai wannan akwai gilashi a tsakanin su , Ya ji 蓷a蓷in ganin ban蓷akin a haka ba dan kome ba sai dan sake samun kusanci da ita a matsayin ta na mai laruri a kuma ba茩on guri da bata kai ga haddace tsarin sa ba bare ta iya yin gaban kan ta a yayin mu'amalar cikin gida . *** Baban Mama . Ta 茩ira sunan sa cikin sanyin Muryar ta lokacin da ta gama sallolin ta tana son fitowa daga 蓷akin ta gaza gano 茩ofar , ga sanyi da take ji yana da蓷a ru蓷a ta , gami da sasu茩a茩茩ar yunwar da ta fara gallabar 拼an hanjin ta , Da sauri ya taso, kasantuwar daman hankalin sa na gare ta , ya fito zuwa 蓷akin ri茩e da Mama wacce take sanya 拼an 茩afafun ta a duk inda ya ajiye nasa , Yana tura 茩ofar cikin rashin sani tana tsaye a wajen 茩ofar ta 蓷an daki fuskar ta , Ashih Ta furta tana murza goshin ta聽 , Da sauri ya saki hannun Mama ya 茩arasa gami da tallafo ta jikin sa ya ri茩o 茩ugun ta ya 蓷ora tafin sa akan goshin ta yana murzawa a hankali Je suis d茅sol茅 Fatima,聽 ban san kina kussa ba , akwai zafi ? T'ai-je bless茅 ? A hankali ta zame jikin ta , Ban ji ciwo ba , ka kaini wajen wuta na ji 蓷umi nan akwai sanyi , Bai zauna a gaban Fireplace 蓷in ba ,聽 yana tsaye akan 茩afar sa ya zura hannayen sa biyu cikin aljihun sweater dake jikin sa ya ce Fatima zani dubo wajen gari ku zauna nan kadda ki tashi , bani jinkirtawa zan dawo , me kuke so daga abinci ? Papa abinci j'ai faim aussi , Mama ta furta haka tana shirin fashewa da kuka , Mama kai ni wajen jakar kayan mu akwai Tourte 脿 la viande,( meat pie )聽 samosa , sai mu ci mu sha ruwa ko ? Eh mama , papa ka kawo jakkar mu聽 , Bayan ya mi茩o mata jakar kayan ta , ta ciro 茩unshin meat pie da samosa,聽 da suke nade cikin takarda , 瞥ar ajiyar zuciya yayi yana juyawa kan 茩afafun sa , Taku biyu yayi ya ji ta 茩ira sunan sa , Baban Mama , ka tsaya ka ci abinci . Kallon ta yayi ya ga ita ma bata kai ga fara cin abincin ba , sai Mama ta dan茩awa meat pie babba 蓷aya , Ku ci abinci Fatima idan na dawo zan ci rabo na , Bata amsa ba ya juya domin ya 茩agauta da ya tafi sanin da yayi idan yammaci tayi sanyin na iya 茩aruwa ,聽 Baban mama Ta sake 茩iran sa Fatima ya ce yana juyowa gami da 蓷ora idanun sa kan fuskar ta , Sunkui da kai tayi , da zata iya hana shi fita zata yi ya bar su su ka蓷ai . Ka dawo da wuri , Shiru tayi tana jiran amsar sa . Da shi kuma ya ji kalmar ta 蓷arsu a ran sa da wani irin yanayi da ya sanya shi murmusawa yana cigaba da kallon fuskar ta daga inda yake tsaye , Saboda-saboda nan ba茩on waje ne ba mu san kowa ba , kar ka da蓷e ko Mama zata nemi wani abu. je serai bient么t de retour Fatima. 聽聽 Yace yana 茩arasa barin falon ya fita gami da rufo musu 茩ofar . Shiru tayi ta kasa cin wani abincin kirki duk kuwa da yunwar da take ji , tana jin kan ta a nesa sosai da 茩asar ta ta haihuwa kewar Nahiyar ta Al'ummar ta , Yaren ta 拼an 茦asar ta na taso mata , yanayin tsananin sanyin Nahiyar聽 nan sam bai mata da蓷i ba , yayi yawa . Ta gwammaci rana irin na Nahiyar ta ,( Africa ) " Tabbas kowa ya bar gida聽 ? Zaman jiran awowi uku da lokaci ya聽 kai gefen la'asar ,nisan sa ya kai na kwanaki uku a wajen Falmata , Ta sauya salon tagumi ya fi iri takwas , Mama kuwa baccin ta take hankali kwance bisa jikin mamar ta , 茦arar bu蓷e 茩ofa ya sanya ta 蓷ago kai gami da maida hankalin ta kachokam kan 茩ofar da fatan jin tashin muryar sa , Sallamar sa ya sa fara'ar da bata da masaniya daga inda ta 蓳ullo bayyana kan fuskar ta , ya shigo da kayayyaki ni茩i-ni茩i a hannun sa , bakin sa na amsa gaisuwar barka da dawowa da take jera masa , Fita yayi tare da sake shigowa da wasu kayan a jakankunan takarda , bayan ya sallami me taxi da ya kawo shi ya rufe 茩ofar tare da 茩arasowa kan kujera ya zauna daga gefen ta. 茒aya daga cikin jakar kayan ya jawo , ya ciro safar hannu sun kai saiti takwas , haka ma na 茩afa ,a jiye su a gefe ya cigaba da zaro manya-manyan rigunan sanyi sun kai guda shida na mata masu launika daban-daban 茩aurara masu inganci Fatima sauya wannan chandail 蓷in da wannan Le pull ta fi nawi , Ta sauya rigar jikin ta da wata lallusar rigar sanyin da aka yi ta da fatar dabbar cikin 茩an茩ara ( Bear ) me 蓷auke da launin fari da ba茩i , da ta kawo mata iya guiwar ta , zame hijabin kan ta yayi ya 蓷ora mata hular sanyi da take maha蓷in rigar , ya zarce da ri茩o hannayen ta ya zira mata safar hannu , Sau茩a yayi bisa guiwowin sa bayan ya kamo tafukan 茩afar ta ya fara 茩o茩arin saka mata safa , Cikin sanyin murya ta ce Baban Mama zan iya sakawa , tare da kai hannun ta ta sau茩e akan na shi hannun da yake sanyi 茩alau saboda yawon da yayi a waje . Muryar shi a 茩asa ya ce . Zan saka miki Fatima hakkin ki ne na kula da ke . A hankali ta 蓷auke hannun ta , ya 蓷ago 茩afar ta ya 蓷ora bisa cinyar sa cikin sannu kan hankali ya sanya mata safar , Nagode ta furta A wani irin yanayi na jin tsantsar kusanci da shi ta tsinci kan ta da bata ta蓳a jin irin sa ba , wani shau茩i me da蓷i ya fara 蓷ibar ta . vous 锚tes belle ( kin yi kyau ) Ta tsinci muryar sa 茒an murmusawa tayi duk da bata ganin sa ta ji tashin muryar sa ya maida mata da martanin murmushin ta , Bayan tarin suturun da ya sayo musu da fiye da rabin su suke masu nawi ( kayan sanyi ) takalma da sauran suturu , da bargunan rufuwa . ya sayo kayan abinci da fiye da rabin su na cikin gongoni ,da kwalaye ne irin wanda yake hasashen zasu iya ci musamman ma Falmata ( shi ai ya saba fita 茩asashen 茩etere ya saba da irin cimakar su)聽 Mama kuwa ya sayo mata kunun yara dai-dai shekarun ta da yake tsammanin zata so shi kasancewar ta ma'abociyar shan kunu . Sai turarurruka da sabulai da sauran 茩ananun abubuwan bu茩atu na gida , sai kuma itacen wutar 蓷umama 蓷aki da ya 茩aro musu , Shi ya ajiye kome a muhallan da suka dace da hakan ya 蓷auke shi har lokacin da duhun dare ya fara shigowa da yake hasashen magariba ta kawo jiki聽 , ya duba lokacin sallah ta yanar gizo ( online prayer timetable聽 )聽 ya ga cewa lokacin sallah yayi . Bayan sun idar da sallar magarib da kan sa ya shiga kitchen domin samar musu da abunda za su ci , Elbow macaroni ya tafasa musu , tare da 拼ar miyar da ya soya ta sama-sama bayan ya ha蓷a kifin gongoni da zallar tsokar nama na gongoni a ciki , nan take kitchen 蓷in ya 蓷au 茩amshin girkin maza . Shi ya zuba musu a plate guda me 蓷an girma suka ci tare baki 蓷ayan su . Bayan sun sallaci isha' zaman shiru ne ya ratsa tsakanin su , saboda rashin sabo da yin hira da juna , Mi茩ewa yayi ya 蓷auki mama wacce ta sake komawa baccin gajiya , Fatima tasso ku tai ku kwanta ke ma kiyi bacci dare ya yi da akwai gajiya ga jikkin mou . Babu musu ta mi茩e ya kama hannun ta zuwa 蓷akin da yake mafi girma , bayan ya zaunar ta bakin gado聽 ya kwantar da mama daga tsakiyar gadon ya mi茩e tare da 茩arasawa gaban fireplace ya kunna musu wuta 茒aya daga cikin bargon da ya kawo ya 蓷auka ya rufa musu , Ki yi mouku du'a Fatima bonne nuit et fait de beaux r锚ves , gya蓷a kai tayi Kan sofa 蓷aya jal da take 蓷akin ya koma ya kwanta tare da rufuwa da bargo聽 bakin sa 蓷auke da addu'o'in neman tsari daga abun cutarwar da daren ke 蓷auke da shi . **** Iskar da take ka蓷awa da 茩arfi tare da sau茩ar dusar 茩an茩ara suka sa birnin na Rochester 蓷aukar matsanancin sanyin da ya sa ba茩i ire-iren su Falmata gaza samun nutsuwar bacci saboda tun baccin farko da ya 蓷an 蓷auke ta da bai kai ko'ina ba ta farka saboda matsanancin sanyin da yake ratsa 蓳argon jikin ta , Motsi ta sake yi a hankali gudun tada Mama wacce ga alama ita sanyin bai dame ta har sosai ba ko kuwa dan ta nitse ne cikin kayayyakin sanyi da bargo ? sake tattakewa tayi a cikin bargon tana jin yadda 茩ofofin hancin ta ke toshewa . Biyamuradi da duk motsin da take yi a kunnen sa , ya bu蓷e kan sa daga cikin bargon sa , tare da mi茩ewa ya zauna , Ta hasken 茩wan fitilar gefen gado da bata cika haske ba ya hango yadda ta cure tana rawar sanyi , Kumama ce , bata son sanyi ya kitsima haka cikin ran sa聽 , Mi茩ewa yayi 蓷auke da bargon sa ya 茩araso bakin gadon Falmata wacce tayi lamo tana saurarar takun 茩afar sa cikin ran ta tana kitsimawa , Ashe shima ya kasa bacci ,?聽 Haba me ake da wannan irin sanyi kamar cikin firiji ? Zuciyarta ta buga 蓷as聽 Lokacin ta ji hawowar sa kan gadon , bata yi aune ba ta ji kwanciyar sa ta bayan ta , hannuwan sa ya kai ya zagaye ta da su , ya zarce da sake matso da mama jikin Falmata , ya yi amfani da hannun sa guda wajen sake rufa musu bargo . Lamo tayi tana sha茩ar 茩amshin turaren jikin sa , bata ce kome ba kamar yadda shi ma bai ce 茩ala ba , Sannu kan hankali 蓷umin numfashin su ya gauraya tare da taimakon 蓷umin jikin su da yake ratsowa ta cikin suturun jikin su, tsanani sanyin da suke ji ya ragu , bacci mai da蓷i da nutsuwa ya yi awon gaba da su baki 蓷aya . Washegari Tara na safe ta yi musu a ofishin Dr Williams inda bayan gaisuwa Suka makala pilot-in-ear a kunnuwan su聽 Da bayani game da irin matakin cutar Mama ya fara , yana cigaba da bayani kan magungunan da zasu 蓷ora ta akai wanda zai iya taimakawa wajen rage tasirin cutar da tsananin ta duk cikin harshen turanci Falmata da ta 茩osa ta ji maganin da zai warkar mata da Mama ta katse Dr Williams da tambayar sa cikin harshen farasanci Dr la dr茅panocytose peut-elle 锚tre gu茅rie? ( shin cutar amosani jini tana warkewa ? ) Kai tsaye ya amsa mata da cewa cutar amosanin jini a halin yanzu ba'a kai ga gano maganin ta da za'a sha a warke ba a duniya sai dai hanya guda da ake yin amfani da ita wajen samun warakar cutar , hanyar ita ce dashen 苼argo , Ana yin dashen 苼argo/dashen 茩wayoyin jini ga masu 蓷auke da cutar amosanin jini daga kan masu shekaru bakwai zuwa sama , 聽 ana amfani ne da 蓳argon dake jikin 蓷an uwa/拼ar uwa na jini ga marar lafiyan wanda jinin su ya zo 蓷aya . Duk da ba'a da tabbaci na samun waraka baki 蓷aya ga mai 蓷auke da wannan cutar bayan an masa dashen 蓳argo amma fiye da kashi hamsin na wa蓷anda aka yiwa aikin an samu nasara sun samu waraka daga cutar baki 蓷aya, Sai dai akwai yiwuwar hatsari a yayin aikin da bayan yin sa , zai iya kawo hauhawar wasu cututtukan da yake tsakanin Rayuwa da Mutuwa da kashi hamsin cikin 蓷ari . Bayan 蓷an uwa ko 拼ar uwa shin mahaifiya zata iya bada kwayoyin jinin/苼argon ta ga 拼ar ta ?? Baza ta iya ba聽 , sai dai idan an rasa 蓷an uwa ko 拼ar uwar da suka haurawa shekarun balaga , ana amfani da 茩wayoyin jinin cibiya na 蓷an da ke cikin mahaifiyar sa da ya kasance 蓷an uwa ne ga shi marar lafiya da jinin su ya zo 蓷aya . A hankali Falmata ta zare Ambassador dake kunnuwan ta , hawayen idanun ta na sauka bisa kan hular Mama da take cinyar ta , Ashe cutar Mama Babba ce daga cikin manyan cutuka , ?聽 Tausayi me tsanani ya taso mata yana kassara gabban jikin ta . Rungumeta tayi tsam a jikin ta , tana shafar bayan ta . Mama bata da dan uwan da zai iya sadau茩ar da jini da 蓳argon sa a gare ta , a halin yanzu Bani da damar sadau茩ar miki da jini ko 蓳argo na Mama . Amma ina da damar zama uwar jaririn da zai sadau茩ar miki da jinin sa Mama tun kafin ya zo duniya .. Jama'a duk mu diba , shekara biyar yau a cikin wata na goma , shugaban mu babban mu ya nuna hanya na gyaran 茩asar mu , Sannu , sannu ,kwana nesa , sannu bata hana zuwa , Allah kare 茩asar ta mu Rabbana dai ya ri茩a Hehehe ,ina 拼an 80s ? Ku zo mu chafke , wayyo jiya ba yau ba! 馃槩 duk wacce /wanda bai san lokacin da aka yi yayin saka wa茩ar nan ta 拼an matan Niger a gidan Tv Nigerian television Authority Ba,? Ko kuwa mutum yana 蓷an 蓳ingilin yaron sa ko mitsilar yarinya , ko kuma jaririya/jariri ? 馃槀 to ya gusa daga nan manyan yayun sa ne ke baje koli . Ehe ,( ah kai 茩annen mu 拼an 2000 Ayi shiru kawai a wuce wajen nace ayi hiru babies聽 ) A ssalamu Alaikum waramatullah Yan uwa maza da mata , ina mika sakon gaisuwa tare da fatan alheri agare ku baki daya . Kamar koyaushe ina mai sake mika godiya ta bisa ga yadda kuke bayyana kaunar ku tare da jimirin bibiyar littafin nan duk kuwa da irin tarin tsaiko da tsaye-tsaye , tafiyar tsutsa kai har ma da ta kunkuru wani zubin ma ana taba salon takun hawainiya a yayin rubutun nan lol # duk babu kome Tafiya sannu bata hana zuwa insha Allah wataran zamu kai karshen sa . Masu kiran waya tare da barmin sakonni dubiyar yara , Nagode kwarai kwarai Alherin Allah ya cimm muku a duk inda kuke . Jikin yara Alhamdulillah sun warware . Idan nace ina da tarin aiyukan da suke katange ni daga taba wayar kan ta , za ku iya cewa ba gaske ne ba , sai dai hakan ba zai taba zama bakon lamari ba ga Mamar Yara , yar kwadago , kuma daliba , huh ! Nago                     [10/16, 8:19 PM] +234 803 420 3549: MAFARI ( Hargitsin Rayuwa ) Umm'muaz 36 Doctor Hamza tare da wasu abokan aikin su,  da wasun su ke a zaune wasu na tsaye  daga cikin ofishin shugaban su kuma tsohon malamin wasu daga cikin su a zamanin karatu , Professor Talba Garkiɗa, A zahiri a nutse yake ya bada hankalin sa da ƙululun idanun sa bisa kan Prof wanda ya dilmiye sosai cikin yin bayanai game da cutar da take damun matar dake cikin mawuyacin hali a ICU da jagorancin duba ta ke a hannun mutane huɗu daga cikin su . Sai dai a baɗini cikin hankalin sa sam babu nutsuwa , babu jin daɗi bare kwanciyar hankali a tun jiya da ya amsa ƙiran prof . Nisawa yayi yana sake jin yadda zuciyar sa ke ƙara ƙuntata , wai shikenan domin Ubangiji Allah yayi umarni 'ya'ya su bi iyayen su sai kuma su iyayen suyi amfani da wannan dama wajen cusgunawa 'ya'yan su ? Ah cusgunawa mana , idan ba dai Baba ya so sanya shi a tsaka me wuya tare da damal-mala masa ginin tsarin rayuwar da ya riga ya tsarawa kan sa ba wanne dalili ne zai sa shi ya ɓaɓ-ɓako masa da maganar ƙarin aure ?? Wai fa ƙarin aure ? Shi lamarin ma har kawo yanzu mamaki yake bashi , yana tantamar anya ma kunnuwan sa sun ji zancen a dai-dai ? Idan ya tuno da yadda kalaman suka fito daki-daki tare da sake jaddadawa akan babu shakka umarni yake ba shi har ma kuma ya riga ya sama masa matar , sai ya ji wani mololon baƙin ciki ya tokare shi , shi fa ba yaro bane yanzu. Shi kenan haka zai yi rayuwar sa tare da mata har biyu da ba zaɓin sa ba a matsayin matan sa ? Safiyya da kan ta ba zaɓin sa ba ce , aure ne mai kama da na dole aka liƙa masa shi kuma ya sa hannu dole ya amsa daɗi da ƙarawa lokacin yana a tsakiya da jin takaicin ɗiya mace , domin haka yasa shi gaza musantawa . Yanzu kuma da yake ɗan lallabawa da Safiyyan da daɗi ba daɗi suna zaman su tana faran ta masa dai-dai gwargwado shine kuma za'a sake bijiro masa da wani auren ? To a dalili da me ? Shi a tsarin rayuwar sa babu saki ba kuma gurbin mata biyu . Mace ɗaya tal ta ishe shi ,shiyasa ma ya bada kai yana lallabawa da wacce ta zama ƙaddarar sa ,  rabon sa duk kuwa da cewa ba zaɓin sa bace . to yayi yaya da mata biyu ? Jera su zai yi yana kallo ? Ko kuwa a wuya zai rataya su yana yawo da su suna reto ?  Ɗan tsaki ya saki a hankali . Lokacin da ya fahimci professor Garkiɗa ya kammala jawabin sa ba tare da shi ya fahimci kome ba , alhalin kuma musamman yayi tattaki ya zo domin ya saurari koyarwar duk da cewa kusan abunda ya riga ya sani ne zai sake sanar da su , to amma shi ai maye ne akan neman ilmi kome ƙanƙantar sa , hakan ya sa shi yin zarra a cikin abokan aikin sa masu matsayin karatu irin nasa , Ai ga irin ta nan tun kafin a je ko'ina ya fara sururucewa akan tunanin rayuwa da mata biyu , anya kuwa zai iya ? Miƙewa yayi yana jin takaicin rashin saurarar koyarwar da prof yayi musu . Bayan fitowar su daga ofishin suka tsaya shi da abokin aikin sa suna tattaunawa . Mata biyu ne suka doso wajen hannuwan su riƙe da kayayyaki ,  kondunan zuba abinci da wasu tarkace , Karaf idanun sa suka sauka akan matar rannan , Tun a ɗan nesa yake nacewa kallon kamannin ta da ke kamanceceniya sosai da na Khaalty Rahima , ba su da wata maraba , sai tsabar tsufa da wani irin duhu da wannan tayi marar kyaun gani, tabbas ko da khaalty Rahima na raye bai ci ba ace tayi wannan tsufan, dududu shekaru biyar zuwa shidda ta ba shi , Bai farga ba suka gota shi , da sauri ya bi bayan su ba tare da yayi sallama da Abokin sa ba    Yana son sanin wacece ita , ? Sallama ya dunga rangaɗa musu har baki biyu babu wacce ta juyo a tsakanin su sai da yayi ta uku , Ɗayar kakkaurar matar baƙa gajera ta juyo , " Au nan ne  ? Da mu ne ? Ca nake a iska nake ji , "Sannu Mama Da abokiyar tafiyar ki na ke son yin magana , ya furta haka yana nuna bayan ta da ta ɗan yi gaba batare da ta tsaya ba tana cigaba da tafiyar ta , takawa yayi ya bita ganin tana shirin shan wata kwana . "Hajiya sannu , " sannu Hajiya ," Shiru ya ji tayi , Dan haka ya ɗaga taku ya sha gaban ta , Da sauri ta ɗago kan ta , ta kai duban ta kan shi , Kallon-kallo suka yi , jakar kayan da yake hannun ta ya sulluɓe ƙasa , Lokacin da ta wara idanun ta dake nuni ƙarara da halin ruɗanin da zuciyar ta ke ciki  ,    Motsa baki tayi da sautin ya gagara fitowa  , sai kuma tayi saurin kauda kai . ,"Khaalty Rahima ?? Yace da wani irin maɗaukakin sauti , da ya zarce da wata ƴar dariya da ke nuna tsantsar farin-cikin da ya kawo masa , Hannuwan sa biyu duk ya kai ya kamo nata hannuwan dake cikin hijabi ya riƙe , " Malam lafiya kuwa ? Matar da take abokiyar tafiyar ta ta furta haka lokacin da take ƙarasowa tana bin su da kallon mamaki da manyan idanun ta . Bai kula ta ba ya jijjiga hannun ta dake cikin nasa , ,"Khaalty Rahima tahadah 'iilaya rja'a ,    Ya furta hakan yana sake kallon ta da ta sunkui da kai tayi ƙiƙam kamar bata jin sa , bai yi aune ba ta warce hannun da ƙarfi , ta sunkuya tana tattara kayan hannun ta . Durƙuso yayi yana taya ta kwashewa ,tare da leƙa fuskar ta yana son sake ganin ta . "Khaalty Rahima" ya sake ƙira da wata irin murya , fuskar sa na nuna tsantsar damuwar da ta maye gurbin farin cikin sa . "Yau ga ikon Allah Malam kurma ce fa kake ta faman yi mata magana , ' Tare suka miƙe da ita , da wani yanayi na firgici ya juya yana kallon matar . "Kurma ? "Eh kurma ce mana , hala ka san ta a wani waje ? Mamar Bulama da yawan gidajen masu kuɗi take ,  Ai manyan gidaje ɗaya-ɗaya ne a cikin garin nan da bata yi aiki ba , har gidan inn-in wannan mashahurin attajirin mai tashen kuɗi na bala'i da masifa , bani sunan sa ma ? Ga shi da suna mema sunan na sa ??,' ," kika ce kurma ce ? Mamar Bulama ? Wacece ita ? Ba gaskiya bane wannan ƙanwar Mama ta ce . Juyowa yayi , sai dai ko alamar ta bai gani ba a wajen , " ina take ?," ",Tayi tafiyar ta , ai kaga halin ta na miskilancin da yake sa ake tisa ƙeyar ta a kore ta daga gidajen da tayi aiki , miskilanci da faɗin rai na tsiya , to Allah na tuba kana talaka faƙiri mai neman na sawa a bakin salati ina kai ina faɗin rai ? Wa kuma zaka gwadawa ya ɗauka?  Gidaje daban-daban huɗu muka yi aiki tare , biyu akan halin ta aka ƙore ta biyu akan wannan ifiritun ɗaya-ɗayan ɗan nata Bulama haba me ake da batsal-tsalewa irin ta Bulama ya ɗan yayen biri ? . Bai ƙarasa sauraron matar da take tsakiyar yi masa bayani har bakin ta na kumfa ba yayi wucewar sa ya bi sawun ta ,   Cikin ran sa yana faɗin ",haba me ake da ɗan banzan surutu marar ma'ana ? Duba ta yayi har ɗakin da ya san marar lafiyar da suke zuwa wajen ta na ciki amma bai gan ta ba. Bai kuma tambayi matan da ya tarar a ɗakin ba da ko alamu basu da nasaba ta jini da ita , dan haka sai ya koma. kichiɓus suka yi da matar da ya baro a waje , ," ka same ta.... Da hannu ya dakatar da ita , alamar tayi masa shiru  ya wuce cikin ran sa yana bawa kansa tabbaci babu shakka Khaalty Rahima ce , ita ya gani Ƙanwar mamar sa ce da kusan tare suka tashi  , tunda ya buɗi ido ya gan ta a gaban iyayen sa kafin daga baya kaddarar da bai san ta mecece ba ta gifta tsakani ta raba su . Sai dai koma menene yana ganin yazo ƙarshe , zai bi kuma duk hanyar da ta dace domin dai-daita rayuwar iyayen nasa daga walagigi . Kai tsaye wajen motar sa ya nufa zuciyar sa cike da tunanin hanyoyin da zai bi domin gano haƙiƙanin rayuwar da Khaalty Rahima take tsawon shekarun nan, shin ita ce ko kuwa ba ita bace ? Khaalty Rahima bata da wata larura da ta shafi ji ko gani , ance wannan kurma ce ?? Tada motar sa yayi , zuciyar sa maƙare da wasi-wasi , wajen Amne yake da burin zuwa a yau ɗin to amma yadda yake jin zuciyar sa a yanzu bai son kome illa ya kaɗaice . Yana isa gida kai tsaye sashin su Rahima ya nufa saboda yunwa da yake ji tana ƙwaƙular ƴan hanjin sa , Da sallama ya shiga falon , idanun sa suka sauƙa akan ta da ta juya baya tsaye a gaban hoton ƴar yarinyar da bai kai ga rarrabewa ɗiyar wacece a tsakanin Hafsa da Zainab ba ? Zama ya yi akan kujera tare da yin baya da kan sa ya jingina da kujerar "Rahima idan akwai abinci ki kawo min , idan kuma babu ki dafa min Noddles yanzu ina jin yunwa sosai ki haɗo min da tea .' Numfashin ta ne yayi sassarfa lokacin da sautin muryar sa ya sauƙa a kunnuwan ta, shikenan addu'ar ta bata karɓu ba , domin kuwa tunda Rahima ta tabbatar mata da cewa hutu ya zo zai ya koma garin Abuja inda ya koma aiki da zama baki ɗaya tare da matar sa , take addu'ar Allah ya raba ganawa a tsakanin su har ya gama hutun sa ya koma . To sai dai addu'ar ta ta a iya ranakun jiya da shekaranjiya tasirin ta ya tsaya , domin ga shi yau ko azahar bata yi ba Alƙadarin ta ya karye , Ita kunyar sa take ji , kunya mai tsanani kuwa , kunyar abunda ta aikata , me zata ce masa ? Da wanne ido zata dube shi , anya duniya da gaskiya ita tana da tsaurin idon sake kallon sa ? "Rahima baki ji na ? Satar kallon inda yake Yakaka tayi ta gan shi har yanzu yana yadda yake kan shi a kwance bisa kujerar ya miƙe ƙafafun sa . Ba tare da ta juyo ba ta kama hanya da ƴar sassarfa da nufin barin wajen tsawar da ya daka mata ya sa ta dakatawa tana jin yadda zuciyar ta ke tsananta bugu . "Rahima yaushe kika zama haka , marar ɗa'a ? Ni nake yi miki magana kina tafiyar ki ?  Zo nan . Juyowa tayi a hankali , ta tsugunna a wajen da take , muryar ta tana sarƙewa tace "Ba-ba Rahima bace ni ce Yaya Dakta . Tamkar a ire-iren shuɗaɗɗun mafarkan sa da ya saba yi a shekarun baya ya ji sautin muryar ta , dan haka ya buɗe idanun sa da suke lumshe a hankali . "Rahima zo nan nace " Ya sake maimaitawa cike da burin son kawar da mummunan tunanin da ya bijiro masa da sautin ta a yau . Ni ce Yaya dakta ta sake maimaitawa tana kif-kifta ido daga inda take . A wani irin yanayi ya yunkuro kamar an tunkuɗo shi , ya zauna da kyau lokacin da yake ɗora idanun sa akan ta , da ta sunkui da kai ta ƙi kallon sa illa bakin hijabin ta da take wasa da shi a hannun ta , Ita ce ? Me ya dawo da ita ? Me ta zo yi nan ? "Ke ce wa ? Ya furta hakan da wata buɗaɗɗiyar murya me amo da ya sa Yakaka yin rau-rau da idanun ta da suka kawo ƙwalla , Shiru tayi , "Ke ce wa nace ? Me kika zo yi gidan nan ? ,"Ni ce Yakaka ."   Ta bashi amsa cikin sanyin murya ba domin tana da yaƙinin bai gane ta ba , sai domin yunƙurin ta na ganin ta wanke kan ta . Miƙewa tsaye yayi yana jin yadda wani irin bacin rai da ya sauƙo masa tun daga tsakar ka yana neman rufe masa idanu ,  "Tashi ki bar gidan nan ," ko kuwa na sa maigadi ya fita da ke , nan da kike gani ", ya buga ƙafar sa guda a dandaryar falon cikin yi mata nuni , "   Ba gidan Karuwai bane , ba kuma gidan giya bane , tashi nace ,"    Ya kwatsa mata tsawa   Tsawar da yayi mata bata razana ta ba , bata kuma huda zuciyar ta ba irin kalmar karuwa da gidan giya da danganta ta da su , A hankali ta ɗago kan ta , idanun ta suna zubar ƙwalla tace , ",Yaya Dakta kayi hakuri dan Allah na san nayi kuskure amma wallahi ba karuwanci naje ina yi ba makarant.... ,"Shut up, "Ki tashi ki fita nace , ya furta hakan yana kusanto ta da takun ƙafar sa  , ," Big Bro , Ya tsinkayi muryar Rahima daga bayan sa , Ƙarasowa tayi tana raba ganin ta a tsakanin su biyun , da sauri ta ƙarasa wajen Yakaka wacce zuwa lokacin kuka take haiƙan , ta ɗago ta tsaye "Big Bro , Mamar Mama ce fa Yakaka , bata mutu ba , kai ma kayi zaton Fatalwa ce kamar yadda ta tsorata ni da farko ko ? , "Rahima ki min shiru , yace yana nuna ta da allin ɗan yatsan sa , goshin sa a tattare da mabayyanin ɓacin rai . ,"ke ki tattara ki bar gidan nan yanzu-yanzu , kar ki ƙara minti goma idan ba haka ba kuma zan sa a fitar da ke ," Da sassarfa ya bar falon , Babu shakka kunya tayi ƙaranci a zamanin da muke ciki , idan banda tsagoron rashin kunya ita wannan yarinyar har tana da ƙarfin guiwar dawowa cikin gidan da ta gudu ta bari ?? Shin da wata alaƙa ta jini ne a tsakanin su bayan taimakon da yayi mata da ta saka masa da tarin butulci ,? Da har kuma yanzu zata ɗebo ƙafafu ta zo gidan su to a matsayin wa take ? Kuma gurin wa ta zo ? Har ta gama barikin ne ta gaji ta dawo ? Zaton ta nan matattarar karuwai ne ?  Ko kuwa har auren nasu da uban ƴar ta ta ya ƙare ne ? Dole ta bar gidan kamar yadda tayi a baya,  tayi nesa da shi da dangin sa domin mumini ai baya sanya hannun sa a ramin Macijiya sau biyu . Ba zai taɓa saurarar ta ba , ita ɗin zantukan bakin ta ai duk ƙarya ne , da yaudara , kirkin baka ne da ita tare da ladabin banza . Runtse idon sa yayi yana tura ƙofar sashin sa da ƙarfi , ɓacin ran ganin ta yana sake hauhawa a ran sa hatta yunwar da yake ji tayi ƙaura . ,"Rahima dole na tafi tunda Yaya Dakta ne da kan sa ya kore ni kin manta shi ne ya fara kawo mu ? Dalilin sa muka zo gidan ku Rahima bani da ikon cigaba da zama ," Yakaka ta furta hakan tana shiƙar kuka lokacin da take jawo jakankunan kayan ta , Kukan ta daga ƙasan ran ta yake , kukan tausayin rayuwar ta tare da nadama ,   ina zata je ? Tun zamantowar su 'yan gudun hijira nan gidan ne kaɗai mafakar da suka tsaya cikin ta ba tare da ƙalubale ya cisgesu ba har sai da ita da ta sanya kafafun ta da kan ta ta bar mafakarta , Tayi zaton kome zai zo mata da sauƙi zaton ta zai yi saurin yafe mata , tayi tunanin zai tare ta da yawan ƙaunar nan tare da tausayin da ta san yana gwada mata can baya , har ma tana sanya ran cigaba da samun kulawar sa kamar farkon fari , Ashe dama ta riga ta kufce mata , ta riga ta ɗibga kashi a inuwar da ta huta , ashe ita ɗin yanzu wulaƙantattace a wajen sa ? Ashe yanzu ita abun kƴamata ce da bata wuce a kore ta ba ? Babu shakka ba'a ɓari a kwashe du , hangen hadarin nesa kuma ya sanya ta damal-malewa cikin kashi . Ɗauki take nema , so take ta samu wanda zai dube ta ya fahimce ta ba tare da ya aibata ta da laifin da ta riga ta aikata ba ,  ba tare da wani hukunci yayi tsalle kan ta ba sakamakon abunda ta aikata da bai wuce Kaddarar da zata iya hawa kan kowanne ɗan Adam ba . Malama Maryam ita ce ɗaya jal wacce ta sani da tashin farko bayan sanin laifin da ta aikata ta tausasa mata , a yanzu kuma bata nan , tayi komawar ta garin su tun kwanaki biyu da suka wuce . Shin Mutane ba za su mata uzuri ba ? Ashe haka halli  'yan adam yake ?? Da wanne zata ji ? Ita kenan haka guguwar Rayuwa zata cigaba da walagigi da ita ? Yanzu ina zata ? "Kar ki tafi Yakaka  tsaya ina zuwa . Rahima ta katse ta bata tsaya jiran amsar ta ba ta fita da ɗan gudun ta , bata tsaya ba , ta cigaba da jan  baccon ta da yafi ƙarfin kinkimar ta , tana yi tana rera kuka da murya mai ban tausayi . " Yakaka , Yakaka ki tsaya , kar ki tafi nace ki zo Baba yana ƙiran ki .' Kanta a ƙasa tana sharar ƙwalla ta shiga falon Prof , da ta tadda shi kamar koyaushe a zaune , muddin zai miƙe tsaye sai da sanda mai ƙarƙo . Muryar ta tana rawa ta gaida shi , ya amsa yana nazarin ta , ," Me ya faru zaki bar gida 'yata ,?  meye dalili ? Muryar ta na rawa tace "Yaya dakta ne yace na tafi  . Ya gane wanda take nufi dan haka ya ɗan yi jim cikin ransa yana sake ganin dai-dai kan ƙudirin sa . "Ki koma ciki , nan gidana ne ba na wasu ba , dan haka babu wanda yake da damar korar ki , kin ji ko ? ',To Baba , nagode ," ", Madallah ku koma ciki ,' Bayan tafiyar su ya ɗau wayar sa tare da ƙiran Doctor Hamza wanda tunda ya shiga sashin nasa ya gaza aikata kome illa kai-kawo da yake yi , zuciyar sa na cigaba da tafasa , Bayan ajiye wayar sa , sashin Prof ya tasamma , inda ya tarar da shi yana  tsimayen sa , bai saurari gaisuwar da yake yi masa ba , ya fara da tambayar sa fuskar sa na nuna ɓacin rai "Me yarinyar nan tayi maka zaka kore ta ? Da sauri ya ɗago kan sa yana duban Baba , a zaton sa yau ta zo , sannan Baba bai ma san da zuwan ta ba , ashe ba haka bane . Shin ƙarar sa ta kawo ? Babu shakka babu kome a bariki sai darussan da ke koyar da tsaurin ido tare da rashin kunya , Shiru yayi , ganin yayi shiru ya sa Prof  sake jefa masa wata tambayar "Ko kuwa ta aikata wani abu da ba dai-dai bane ? Ko tana kan aikatawa da ta cancanci kora ? Shiru Doctor Hamza ya sake yi , kai tsaye ba zai ce ga abunda ya hana shi ya ce kome ba , Bazai ce ga dalilin da yasa ya gaza bayyana laifin ta da yake sirri ne a gurin sa wanda yake tunanin a iya tsakanin su biyu yake,  da kuma can inda tayi rayuwar bariki , sai dai hankalin sa yafi tafiya akan ya rufawa ƙaryar sa da yayi a baya asiri ne,  sanin da yayi Ƙarya wata mummunar ɗabi'a ce da iyayen su suka wanzu suna hanin su da aikatawa , "Idan baka da wani dalili ,kar ka sake korar ta , ita ɗiya mace rauni ne da ita a koyaushe , a kuma ko'ina tana buƙatar matallafi ne cikin rayuwar ta , ' " Wanda daga zarar ta rasa mai tallafar ta zata iya faɗawa kowacce irin mummunar rayuwa  , yan gudun hijira su ma mutane ne kamar kowa walaƙanta su abune marar kyau , ka kiyaye . "Zan kiyaye Baba , *** Yakaka tana komawa cikin gida bayan Rahima ta kama mata kayanta sun mayar su ɗakin da cikin sa suka  zauna ita da Falmata tun farkon zuwan su gidan , muryar ta a ɗan dishe ta ce   " Rahima yaya Dakta fa yunwa yake ji , da farko da ya shigo yace ki masa girki ,   Zama Rahima tayi a bakin gado tana ɗan riƙe kanta ,   "Yakaka wallahi kaina ciwo yake ba kaɗan ba , yau nasha yawo a School ( makaranta ) taimaka ki ɗan dafa masa ko ƴar indomie ce . Bata ƙarasa zancen ba yakaka ta nufi ƙofa , tana amsawa da "To yanzu zan yi ," Bayanta Rahima ta bi da kallo cikin ranta tausayi ne me tarin yawa , Yakaka mai kirki ce kaddarar Rayuwa ce ta faɗa mata ta dalilin raunin Ilmi da wayewar ta . Ita da aka ce ta dafa indomie sai ga ta ta zage damtse wajen girka lafiyayyar jalloup ɗin Spaghetti da ta sha niƙaƙƙen nama da kayan ɗanɗano , cikin sauri da azama take aikin dan haka bata ɗau ɗogon lokaci ba ta kammala , ta tafasa shayi ( tea ) da ya buƙata ta adana su a mazubi me kyau ta ɗora bisa ɗan faranti , Zuwa tayi ta samu Rahima tana bacci , bata son tashin ta domin kar ta ƙara mata ciwon kai . Dan haka ta fita daga ɗakin ta koma kitchen tayi tsumu a tsaye hankalin ta ya rabu kashi biyu , tunanin Dakta da yace yana jin yunwa da kuma tsoro da take ji na kai masa abincin , Tayi tsayuwar kusan mintuna uku ta gaza ɗaukar abincin kafin daga baya ta gyara zaman hijabin ta ta ɗau tiren tare da nufar sashin nasa da ba baƙo bane a wajen ta , Cikin sanɗa take tafiya lokacin da ta shiga sashin nasa a yunƙurin ta na son ta shigar masa da abincin ta fita ba tare da ya san ita ta kawo masa ba , Ta zo dai-dai ƙofar tayi tiris ganin ƙofar shiga falon nasa a rufe , ajiye tiren tayi , tana tunanin yadda zata yi ? Wata dabara ce ta faɗo mata , dan haka ta ɗan sauƙe ajiyar zuciya kafin ta kai hannu ta ƙwanƙwasa ƙofar da ɗan ƙarfi , tayi wuf ta juya da saurin ta , garam ! ta ji tayi karo da mutum . Da sauri ta ɗago kanta ganin fuskar sa a murtuƙe yana jifanta da mummunan kallo ya sa ta haɗiyar yawun tsoro , ", Un- um daman Yaya Dakta abincin ne , Un Rahim.. ,"Wuce ki bar nan bana so na sake ganin fuskar ki . Yace da maɗaukakin sauti , Sum-sum ta ratsa ta gefen sa da yayi banga-banga yaƙi matsawa tamkar mai shirin jibgar ta ta bar wajen har tana haɗawa da ɗan gudun ta bayan matsanancin bugu da zuciyar ta ke yi . Sanin darajar abinci ya sa shi ɗaukar abincin da ta kawo masa ya shigar da shi falon nasa ya zauna tare da ajiye ledar da ya sayo abinda zai ɗan ci , Dafadukar shinkafa ce irin wacce aka cika mata ƙaƙale da launi ruwan ɗorawa shar ,  da ya taka takanas zuwa shahararren gurin sayar da abinci da ake ji da shi a garin ya sayo . Loma ɗaya-biyu yayi yaji abincin bai masa yadda yake so ba , sam shinkafar ma bata dahu sosai ba a bakin sa , shi yafi son yaji abinci ya dahu sosai ko shinkafar ce yaji ta suɓut-suɓut tuɓus-ɓus daɗin tauna , ba irin wannan dahuwar ƴan gayun ba,  da yake hasashen rabin shinkafar sai dai ta ƙarasa dahuwa a cikin sa . Rufe abincin yayi ya ɗan ture gefe , yayi jugum a zaune , yana tunanin matan zamanin gaba kamar nan da shekara hamsin anya za'a iya cin girkin su ? Ko Amne da take ba tsohuwa tukuf ba salon girkinta ya banbanta dana yaran mata irin su Hafsa, zainab ,Rahima a bar batun Safiyya wannan ba abunda tafi ƙwarewa akai irin Kwaɗon ganyen salad da take cin sa kamar me . Ɗan satar kallon girkin da Yakaka ta kawo yayi ta wutsiyar idon sa , tsaki yayi tunowa da yayi duk kanwar dai ja ce da girkin su Rahima da na wannan da ya raina dahuwar tasa  . kasa jure yunwar da take sasuƙar sa yayi dan haka cikin yanayin,  ya na iya ?  Ya ɗauko tiren abincin zuwa kan teburin gaban shi , Sai dai Yana ɗora ido akan abincin ya haɗiye yawu , da sauri ya ɗau chokali yayi bismillah ,gami da kai lomar farko bakin sa , Bai saurara ba cikin nutsuwa ya dinga aikawa hanjinsa haƙƙin sa har sai da yaji cikin sa ya samu dai-dai da buƙatar sa sannan ya sarara , a fili yace ", Alhamdulillah wannan ko wacce irin pasta ce haka Rahima ta dafa ? Wataƙila ta zallar Alkama ce ba surki . *** Bayan Yakaka ta idar da sallah tayi addu'o'in da ta saba yi duk bayan sallar ta , Ta waiga ga Rahima wacce ta farka daga bacci "Rahima yaya ciwon kan naki ? Kin ji sauƙi ko ? " Ya ɗan sake ni Yakaka thanks , "Yakaka yawan ibadar ki na burgeni ga yawan addu'o'i da kike yi kin fa kusa mintoci ishirin kina addu'a , Yakaka me kike roƙa haka mai yawa ? Ko dai har da shi ake yiwa addu'ar , Ta ƙarasa zancen tana ƴar dariya tare da kashe idonta ɗaya na ɗabi'a . Ɗan zaro ido Yakaka tayi sai kuma tayi murmushi , "Rahima , Bawa baza'a tambaye shi me yake nema a wajen Ubangijin sa ba , Duk abunda nake roƙa bai wuce neman gafara da samun Rahamar Ubangiji ba gare ni da iyayena da 'yan uwa na ,   Jim tayi kafin ta cigaba da cewa , ,"Ummin mu , Rashin sanin a wanne hali mamana take tsakanin Rayuwa da mutuwa yana matuƙar tayar min da hankali Rahima , kullum roƙon Allah nake ya ƙaddara haɗuwar fuskokin mu , idan kuma ita ma ta rasu kamar Baban mu , ina tsawaita musu addu'ar samun gafara a wajen Allah . Hawayen da ya tsatsafo a idonta ta goge cikin ranta ciwo take ji na rashin iyayen ta . Cikin tausayawa Rahima tace , "kiyi Haƙuri Yakaka , babu shakka abune mai ciwo naka ya ɓata har gara ma ace mutuwa yayi kaga gawar sa aka yi jana'iza aka binne , kowa ma jiran mutuwa yake , " Muma akwai Auntie na takwarata ce sunanta aka sa min , ita ma ɓata tayi tun ma kafin a haife ni , "Amne tana bani labari lokacin tana da ciki na ,  Khaalty Rahima ta bar gida tana yarinyar ta yadda Amne ke bani labari bata ma kai mu shekaru a yanzu ba  , " tundaga lokacin Rayuwar gidan mu bata sake zama dai-dai ba , duk da bansan Ƙhaalty Rahima ba amma labarin kirkin ta da yadda Amne ke ƙaunar ta yasa nima ina sonta sosai , ina kuma so ta dawo wataƙila rayuwar gidanmu ma ta dawo mai daɗi , " Cike da jimami da tausayi Yakaka tace ,    " Allah sarki Khaalty Rahima Allah ya bayyana ki daga yau zan dunga saka ta cikin addu'o'i na .   " Nagode Yakaka , duk ranar da muka je gidan Amne tare zan sa ta nuna miki hoton Khaalty Rahima . Cikin zumuɗi Yakaka tace "  yaushe zamu je Rahima ? Ina so naje na gaishe da Amne . "Weekend ( ƙarshen sati ) insha Allah . " Allah ya kaimu , Rochester New York City Tafe Biyamuradi Youssouf yake akan titin 3rd Ave, jikin sa sanye da kayan sanyi daga ƙafa zuwa kansa da ya ɗora hular da take da laɓɓa biyu da suka rufe masa kunnuwa elmer fudd da aka fi ƙiranta da Trapper hat   . Hannun sa ɗaya riƙe da 'yar jakar takarda da ya sayo ( Hot chocolate ) mai dauke da tambari tare da sunan kamfanin chocolate and Vines a jiki , domin su ɗumama cikin su ɗumin hot chocolate ya ratsa musu gaɓɓai kafin su fita zuwa cikin asibiti nan da awa ɗaya mai zuwa , Cikin kwanaki biyar da suka biyo bayan zuwan su ƙasar Amurka zuwa ganawar su da likita da duk wasu bayanai da suka samu game da Cutar dake tare da Mama . Daga Biyamuradi Youssouf har Falmata sun rasa karsashi da nishaɗin su , musamman Falmata wacce tundaga wannan ranar take cikin damuwa da tunanin hanyar da zata iya bi domin ganin ta samar da abunda zai zama sanadi na samun warakar cutar Mama da sanyin ƙasar tare da sauyin ruwa suka haɗu suka sa ta ɗan fara kukan ciwo , Sai dai kasancewar nan Amurka ba kamar ƙasashen Africa da basu cigaba bane ta fuskar kula da lafiyar ɗan Adam . Cikin ƙanƙanin lokaci a rana ɗaya aka bata magunguna tare da duk wani taimakon da ya dace a ƙarshe likitan ya gargaɗe su akan kiyayeta daga wannan sanyin mai tsanani , dan haka ciwon bai tsananta ba ya lafa  . Kwanaki biyu Biyamuradi yayi yana tsara abunda ya dace na daga sabon kuɗirin sa , da tunda ya samu gamsassun bayanai daga bakin likitan Mama , Ya dangana da nema mata lafiya a yanzu domin babu damar yi mata dashen ɓargo ko juyen jini da zai iya bata waraka , dole zasu cigaba da haƙuri tare da kula da ita , tana shan magungunan ta har zuwa wasu shekaru nan gaba da za'a samu wani cikin 'yan'uwan ta da zai isa sadauƙar mata da ɓargon sa .   Tun a washegarin ranar ya koma asibiti ɗauke da sabon ƙudirin sa bayan dogon nazari tare da kai komo a ƙarshe zuciyar sa ta amince ya haƙiƙance cewa zai kai Falmata ga Manyan likitocin ido dake Mayo clinic su duba ta , idan tana da rabon gani shi zai yi iyakar ƙoƙarin sa wajen biyan kuɗaɗen da za'a buƙata domin yi mata aiki zuwa kan magunguna domin  samun warakar ta . Babu shakka Falmata ta cancanci duk wata kulawar sa duba da yadda take nuna ƙauna ta haƙiƙa ga gudan jinin sa da yake da tabbacin ko mahaifiyar Mama baza ta so ta sama da son da Falmata take yi mata ba , Sannan akwai wani abu da shi yake ji game da Fatima da ya kasa fasaltawa a zuciyar sa sai dai yana yawan sakawa a ransa cewa saboda irin kulawar da take yiwa 'yarsa ne. Bayan haka Halin mutum yana zama tsani wajen samarwa da mutum Alkairi ko akasin sa , halayen Fatima mafi yawansu masu kyau ne , ƙwari yake yabawa da Yakanah tare da Nagartar dake gare ta .    **** Yau ne Alƙawarin sa da Sabon likitan da zai Fara duba Falmata wacce bata kai ga sanin ƙudirin sa ba , domin bai kai ga sanar da ita ba . Kasancewar ƙarfe uku na yamma shine lokacin da zasu ga likitan hakan ya sa shi fita sayo musu hot chocolate Su sha kafin fitar su domin zai taimaka wajen rage musu jin matsanancin sanyi . Da Sallama ya tura 'yar ƙofar ya shiga inda ya tarar da su a zaune yadda ya fita ya bar su , da ɗan gudu Mama ta taho gurin sa ",Bienvenue Papa, que m'as-tu apporté?  (sannu da zouwa Papa me ka kawo min ?) Rungumar ta yayi suka ƙarasa kan doguwar kujerar da Falmata ke zaune fuskar ta ɗauke da siririn murmushi , ", Sannu da dawowa Baban Mama ,   "Sannu da hutawa Maman Mama , yace da sigar zolaya yana kallon fuskar ta      Hot Chocolate ɗin ya ciro musu gami da sanya 'yan chokula ya sakawa  Falmata nata a hannu, Ya ɗauki Mama ya ɗora a cinyar sa ya shiga bata a baki tana kurɓa a hankali Shiru ne ya biyo baya , ɗumin shayin da aka yi shi da garin koko ( cocoa ) da damammiyar  Madara mai zafi yana ratsa sassan jikin su daɗin sa kuma yana basu nishaɗi , da yasa Falmata bata farga da tayi shan haɗama ba sai da ta ji 'yar robar hannun ta sakayau , ta kai chokalin baki , taji bata ɗebo kome ba . Biyamuradi Youssouf wanda duk idanun sa ke kan ta ya ga irin shan da tayiwa chakulan ɗin, ya kai hannu a hankali ya zare robar daga hannun ta tare da musanya mata da nashi wanda bai kai ga fara sha ba , ", Fatima bois ça aussi ( ki sha wannan ma )   " Baban Mama na ƙoshi fa , nagode .    Ta furta hakan tana jin kunya na taso mata , Murmushi mai sauti yayi , ganin yadda gefen bakin ta ya ɓaci , ya kai hannun sa kusa da fuskar ta , hannun sa na sauƙa a jikinta ta jaa baya da sauri tare da ajiye robar hannun ta ,    "Dakata Fatima , repérer zan ɗagga miki daga fuskar ki ,     Babban ɗan yatsan sa ya kai gami da goge mata gefen bakinta inda hot chocolate ɗin ya sauƙa bata sani ba . Kanta a ƙasa tace   "Nagode . bai amsa ba illa ɗibar chakulan ɗin da yayi ya kai bakin ta ,   " amshi lait au chocolat chaud , buɗe bakin ta tayi cike da kunya ta karɓa , "zan iya sha da kaina . tace masa muryarta can ƙasa , yayi kamar bai ji ta ba ,  tare da cigaba da bata a lokaci guda shima yana sha , bata sha dayawa ba tace da shi ta ƙoshi , cikin nishaɗi ya shanye sauran , yana ƙurewa fuskar ta kallo da take sumul babu ɗigon ƙwalliya , Bayan sun gama , yace mata   "Fatima zamou fita zouwa hospitalisé ku shirya yanzou ,   " Baban Mama zamu sake ganin wani likita daban ko ? Wannan bai ƙware ba sosai ya zai ce cutar Mama bata warkewa bace ? akwai ciwon da bashi da magani ne ?   da wani irin yanayi yake dubanta yadda take maganar cike da son samun warakar Mama ya taɓa ransa , ita bata da wani sauran buri ne a rayuwa da ya wuce lafiya tare da walwalar Mama ? Bata yiwa kanta wani shiri ko tanadi ? Bata da wani buri ne na gina tata rayuwar ? " Doctorat gasskiya ya faɗi Fatima , cutar Mama batta maganin waraka a yanzou sai fa kou ɗaya bissa hanyoyin da ya faɗi da kouma babu dama a yanzou , ba bissa lafiyar Mama zamou tafi hospitalisé ba , Shiru tayi ranta babu daɗi , yaya zai ce babu hanyar samun warakar Mama , shi baya irin tunanin da ita take yi ne  ? Meyasa bazai yi wani yunƙuri ba domin taimakawa gurin samar da yadda zasu yi su tsaretar da Mama daga wannan ciwon me azabtarwa , ?    So take tace masa akwai hanya mana ,  sai dai tana cike da tsoro , da jin nawi tare da zargin ko matsayin da take da shi a wajen sa bai kai wannan matakin ba , mafi girman lamarin ya tambayeta ƙarin bayani , to tace da shi me ? Ko a mafarki bata jin ta san amsar da zata iya ba shi . Cikin sanyin jiki ta tashi , da gudu mama ta sauƙa daga jikin Baban ta ta zo ta kama hannun Falmata , sannu kan hankali tayi mata jagora zuwa ɗaki  , Ajiyar zuciya ya sauƙe bayan shigewar su ɗaki , bai ji daɗin sanyin da jikinta yayi ba kan amsar da ya bata , Mayo clinic Doctor Omer Berat ɗan asalin ƙasar turkiyya ( Turkey ) da aiki ya kawo shi Amurka , shine ƙwararren likitan ido da zai duba lafiyar Idon Falmata , Bayan sun shiga wajen sa tare da taimakon na'urar fassara yare suka gaisa , Babu ɓata lokaci ya nemi da ya fara zantawa da marar lafiyar sa , A hankali Youssouf ya kamo hannun Falmata da take zaune a kujerar da take fuskantar ta shi yace ,   "Fatima ki saurara da kyau likita ke son yin magana da ke kan lafiyar ki . " Lafiya ta ko ta Mama ? "Lafiyar idon ki Fatima . Ya amsa yana sake tabbatar mata , Mayar da hankali tayi ga likitan lokacin da ta ji ya ƙira sunan ta , Ta amsa , tana mamaki daman ita ya kawo asibitin a yau ? Tambayoyi ne sosai Likitan yake yi mata da mafi yawan su Falmata bata da takamai-mai amsar su domin tambayoyin sun shafi asalin dalilin sumuwar rashin lafiyar idon nata da ita bata sani ba , amsar da ta bashi a ƙarshe ita ce   " Je ne sais pas, je viens de vivre dans la cécité , mes parents sont morts sans me dire à quel point j'étais aveugle . ( nima ban sani ba kawai na tsinci kaina cikin rayuwar makanta kuma iyayena sun mutu ba tare da sun bani labarin yadda makanta ta ta samo asali ba . )   Biyamuradi Youssouf da amsar ta ta taɓa masa zuciya , ya sake runtse hannun ta cikin nashi , yana jin yadda tausayin ta ya kawo masa . bayan ɗan guntun rubutun da likitan yayi ya umarci Falmata da ta zo kan ɗan wani gado da yake daga gefe a ofishin ya duba idanun nata , Har bakin gadon Biyamuradi ya kama hannun ta , ya kaita tare da kama mata ta hau gadon ta kwanta  , Doctor Omer ya haska ƙwarar idanun nata da penlight , ya ɗora da tambayar ta ko ta ga haske ? Tace ita bata ganin kome , Cigaba yayi da haska idon yana dubawa , a ƙarshe ya kunna slit-lamp ya dallare mata ido da haske , Wani irin kaifi ta ji ya soki idanun ta da ya sata kifta idanun da sauri tare da kai hannu biyu ta riƙe kanta da ya sara mata , "washh kaina . " Sannu ', ita ce kalmar da Youssouf ya furta da sauri yana riƙo hannuwan nata ya sauƙe daga kan ta ,   Bata amsa ba illa riƙe hannun sa da tayi saboda yadda har yanzu take ji ba dai-dai ba a ƙwarar idanun ta .   Bayan likita ya gama dube-dube a ainashin cikin ƙwarar idanun ta , Biyamuradi Youssouf ya kamata suka dawo wajen zaman su suna fuskantar likitan da yake rubuce-rubucen sa cikin kwamfiyuta , Turo ƙofar ofishin akayi wata mace ta shigo , babu ɓata lokaci ta jagoranci su Youssouf zuwa wani sashi na daban inda aka yiwa Falmata hoton ƙwarar ido aka tura ga sakamakon ga Likitan ta ta kwamfiyuta kamar yadda ya turo musu da bayanan irin hoton da yake so su yi mata ta kwamfiyuta . Kafin isowar su hoto tare da bayanan da duk suka dace sun riga sun iso masa , dan haka bayan ya kammala binciken sa  , ya zunkuɗa yana mai gyara zaman gilashin idon sa , ya shiga yi musu bayani dalla-dallah cikin turancin sa yayin da su kuma pilot-in-ear yake fassara musu cikin faransanci , Iritis shine ciwon da ya haddasawa Falmata matsalar idanu da har ya kai ga ta rasa ganinta , shi iritis wata cuta ce da take samun ƙwayar baƙi/brown na tsakiyar idon ɗan adam , da take kumbura ƙwayar idon , sa ciwon ƙwayar idon da disashe gani ,gaza ɗaukar haske da sauran matsaltsalu da dama , wanda ake iya samun sa ta hanyoyin da suka haɗa da ƙwayoyin cutar maɗamfari ( infection ) , jin ciwo kai tsaye ga cikin ido , kamar bugu zuwa ƙwarar ido na daga kowanne irin abu , da kuma cutar da take kama ƙwayoyin halitta na jini tana kashe su. Bayan dogon bayanin da likitan yayi musu ya ɗora musu da bayani kan matakin da cutar ta kai ga idon na Falmata wanda rashin samun maganungunan da suka kamata a kuma lokacin da ya dace , ya kai ga ta rasa ganin ta na tsawon wasu shekaru  sakamakon mutuwa da wasu daga cikin jijiyoyin ƙwarar idon suka yi . kai tsaye bazai yuwu ba ganin ta ya dawo kamar na sauran mutane masu lafiya , duk da cewa akwai yuwuwar kaso ɗaya bisa uku na ganin nata ya dawo tare da taimakon magunguna da allurai zuwa kan aiki na musamman da za'a iya yi mata a idon idan har magunguna da alluran basu taimaka yadda yakamata ba , wanda zai ɗora ta akai da zarar ya kammala binciken sa a yau . Cigaba yayi da yi musu bayani har zuwa lokacin da ya tabbatar sun samu gamsuwa sun kuma fahimci duk bayanan da yayi musu , da kan shi ya jaa jinin Falmata ya fita da shi zuwa ɗakin gwaji saboda ya auna ya san irin magunguna da alluran da suka dace yayi mata bisa ga mataki na farko . Basu bar asibitin ba sai da aka mata allurai biyu ta babbar jijiyar hannun ta tare da yi mata ɗaya a jijiyar da take daf da idonta na dama , Ba ƙaramar juriya ta nuna ba wajen tsayuwa da tayi cikin nutsuwa aka huda mata jikinta babu zilliya bare ihu da hatta shida kansa likitan sai da ta burge shi sanin da yayi allurar gefen idon tana da zafi  ,        Ya dube ta bayan ya ƙare mata allurar gefen idon ,  " sorry It'll hurt but just for a few minutes .    Gyaɗa kai tayi tana jin yadda idanun nata suka yi nawi ga wani irin yanayi marar daɗi da take ji a idon , " Baban Mama , ta ƙira sunan sa tana lalubar hannun sa ,   Da sauri ya riƙo ta " Na'am Fatima , sannu kina jin ciwou ? comment vous sentez-vous en général ? ( How are you feeling overall ? ) "  Idona yayi jini ne ? "bai yi jini ba Fatima , sannu  .    **** Misalin ƙarfe tara na dare suka bar asibitin bayan sun ci abinci sama-sama daga kitchen ɗin cikin asibiti . Suka yi bankwana da likita omer bisa ga yarjejeniyar sake dawowa asibitin nan da kwanaki huɗu masu zuwa , bayan ya haɗasu da mugunguna ɗore da dokoki da sharuɗɗan da ya gindaya musu  . Baki ɗayan su sun gaji Mama tayi bacci a jikin Babanta , Falmata kuwa tsukun da idanunta ke yi yana damunta wanda yake ta zubar hawaye , gaba ɗaya bata jin daɗin kome , damuwarta ta tayar da Hankalin Youssouf da yake amfani da kalmomin rarrashi iri-iri yana jera mata sannu , har suka dawo gida , kai tsaye ya zarce da mama ɗakin baccin su ya kwantar da ita ya lulluɓa mata bargo tare da kunna hutar ɗumama daki ya fito falo inda ya tarar da Falmata ta rufe fuskarta da hannu biyu , ta jingina kanta da jikin kujerar da take A sanyaye ya ƙaraso wajen fuskar sa na nuna damuwa ƙarara  , Zama yayi a kusa da ita jikin sa na gogar nata , ya kai hannu a hankali ya sauke hannun ta daga fuskar , Hawayen da idanun ke yi ya goge da hankicif ɗin da ya zaro a aljihunsa , "Fatima yaya ne ? Ciwo ne har yanzou ? Kou zamou koma ga doctorat ? " Baban Mama idanuna ciwo suke kamar zasu fita , idona bai taɓa ciwo haka ba , bazan warke ba kar kayi asarar kuɗi dayawa , lafiyar Mama yafi samun lafiyar idona muhimmanci kuma .. "  Shittt , yace yana kai hannun sa kan ɗan bakin ta .   " Fatima baki ji abounda Doctorat ya faɗi ba ? Zaki warke ko ba du ba , waye ya faɗi miki zata zam asara doumun nayi jinyar ki daga jakka ta ? " kiyi ta addu'a Allah shi sa a cimma nasara bissa ga neman lafiyar ki kin ji kou  ? Shiru tayi , ita ganin zancen likitan take soki-burutsu tayaya idanun ta zasu fara gani ? Bayan a iya sanin ta bata taɓa ganin hasken duniya ba . Muryar sa ta katse tunaninta " Kou baki so watarana ki ga fuskar mijinki ? Kou baki so watarana ki ga fuskar ɗiyar ki Mama tare da 'ɗiyan da zaki haifa nan gaba ? Jin ya sosa mata inda ke yi mata ƙaiƙayi sai ta ɗago kanta , ' " inaso , amma nafi son na samu ɗa domin ya sadauƙar da ɓargon sa ga Mama , ta warke kamar yadda likita ya faɗa ,   Sai yayi shiru yana kallon ta da taimakon hasken da bai cika yawa ba da ya hasko daga jikin ƙwan fitilan dake ajiye saman teburin gaban su , zancen ta ya zo masa a bazata , ya ratsa ƙwaƙwalwar sa a jirkitatcen yanayi da ya kasa tantancewa . Ita ma shiru tayi cike da fargabar kasassaɓar da tayi , kada dai tayi masa laifi ? Ko dai zantukanta basu dace ba ? Tayi masa tsaurin ido ko ? Sauƙar hannun sa cikin nata ya katse mata tunanin zucin da take yi  , "Fatima mu tafi muyi sallar isha'i kiyi kwana (bacci ) dare yayi ," A sanyaye ta amsa da "To, Har suka kwanta bacci babu wanda ya kuma magana kowanne a tsakanin su yana tunani, Wayar sa ce tayi ƙara alamar shigowar ƙira , da azama ya ɗauka ganin wacce ke ƙiransa ya sanya shi miƙewa a hankali ya nufi ƙofar ɗakin , ya zo fita ya juya gami da kai kallon sa kanta da tayi lamo cikin bargo kamar mai bacci , ajiyar zuciya ya sauƙe ransa cike da tunaninnika barkatai ya fita gami da jaa musu ƙofar , Falmata wacce duk motsinsa a kunnen ta , ta miƙe zaune gami da yaye bargon , cikin ranta sam babu daɗi gani take kamar ta ɓata masa rai da maganganun ta tunda gashi daga lokacin bai sake cewa da ita kome ba , ko fushi yayi ?  Tashin muryar sa da yake magana kamar a gabanta "kasantuwar ta mai buɗaɗɗen kunne " ya sa ta saurarawa  zagayayyar fuskarta na bayyana wani yanayi irin na wanda aka shammata lokacin da taji yana cewa , "bonjour ma princesse comment allez-vous aujourd'hui mon amour? ( Alo gimbiyata yaya kike yau masoyiya ? ) Cigaba yayi da cewa "Je vais très bien et tu me manques aussi , ( ina lafiya lau nima nayi ƙewar ki )   Ƴar dariyar nishaɗi yayi , kana ya cigaba da cewa , " wannan kalma ke kin ka faɗe ta , ni kouwa gurina ba haka ne ba , duk wani bigeren da babu ke cikin sa wajena daɗin sa ragagge ne , babu kome anan sai matsanancin sanyi tafe da tarin nawi da wahalwalu bisa kaina ,   Murmushi yayi mai sauti , " a gida nake Yarima , ga gurin aikina kuma Mai muƙamin Major , nan kuwa ai ban wucce matsayin bawa dake hidima ga wassu rayukan ba , Gicciyewa yayi ya kishingiɗa yana me cigaba da sauraron ta , " ba domin yanayi da bashi yiwuwa na taho da ke ba, kin sani ban iya tafiya ga nissan duniya batare da ke gefena ba maimounatu ke ai sashi ce daga jikina , Falmata da take sauraran sa , sai ta koma ta kwanta tare da lulluɓuwa ta cure jikinta guri ɗaya ga barin sauraran zantukan sa , zuciyarta ke wani irin bugu da yake tafe da zallar tashin hankali ,   Sunan wacce aka ƙira da Maimounatu tare da irin Kalmomi masu daraja da aka mallaka mata , sun gaftare tare da ruguza duk wani ɗan guntun tunanin banza da ta fara yi ,"Ah to na banza mana , tunda 'yar kulawar da yake bata ya sa ta hasashen hawa wani matsayi da bata kai shi ba a wajen sa ashe ita ɗin ba kome bace face tarin nawi da wahalhalu  . Hawaye masu ɗumi suka gangaro daga idanunta suna ɗiga bisa hular sanyin kan Mama . Maiduguri Nigeria Tun ranar da Doctor Hamza ya gargaɗi Yakaka akan kada ya sake ganin fuskarta bata sake bari sun haɗu ba , Ko muryar sa ta ji yayi Sallama da shi bai cika shigowa ma sashin nasu ba , da sauri zata nemi gurin ɓuya , duk cewa tun daga ranar duk lokacin da ya buƙaci abinci daga Rahima ita take girka masa , sai ita kuma Rahima ta kai masa . Yau Asabar ya shigo gidan da safe misalin ƙarfe tara shirye yake tsaf cikin shirin sa na zuwa ɗaurin auren ƙanin Abokin sa . Yana yin Sallama , Yakaka da take goge Falon bayan ta gama sharewa tayi saurin ajiye moper ( mofi ) ta tsallaka da ɗan gudu ta shige ɗaki ta rufo ƙofar , Hajja da take zaune a gefe tana karin kumallo ta harari bayanta ta wutsiyar ido kafin ta taɓe baki , " Ni hauwa'u naga abunda yafi ƙarfi na , ke kenan kullum a tsalle-tsalle da guje-guje ? Uwa wata tunkiyar da take rawar turke ? Allah ya kyauta . Washe baki tayi tana dariya ,lokacin da Doctor Hamza ya shigo " a ah kaga manya ɗiban farko ,  Babban likita , Fuskar sa ɗauke da murmushi suka gaisa , ba tare da ya zauna ba yace   "Hajja ina Rahima ?   " Yanzu ta hau sama , a ƙira ta ne ? " a ah yi zaman ki Hajja idan dai ta fito ace ta min girki kafin dawowata ta kai min ɗakina . " To babu laifi zan faɗa mata .   " Nagode Hajja . Ya juyawa da nufin fita idanun sa suka sauƙa kan Hoton Mama da tun ranar da ya fara ganin hoton yake son tambayar Rahima 'yar waye ? Ƙwarai hoton yarinyar yake fusgar hankalin sa , Dan haka ya dawo da baya yana tambayar Hajja , " Hajja wannan 'yar waye haka aka samu kyakkyawa  ? Da dariya Hajja ta amsa masa " 'yar wajen Fatima ce ,  Mama sunan ta ai sun ma yi tafiya ne can Amurka ita da iyayen nata . "Fatima ? Ya maimaita , " wacce Fatima Hajja ?  " Ƙanwar wannan yarinyar Yakaka take ko wa ?   'okay , Ya amsa yana barin wajen ba domin ya gane wacce ake nufi ba kai tsaye sai dan ƙiran sunan Yakaka da Hajja tayi . ƙarfe biyu na rana suka shirya tafiya gidan Amne su Uku Rahima , Yakaka da kuma Hajja da itama tace zata je . Shatar shatar adai-daita Rahima ta ɗaukar musu wanda ya tokare daga bakin hanya yaƙi gangarawa kwarin unguwar a cewar sa gargadar cikin unguwar zai ɓata masa mashin , dan haka dolen su suka sauƙa Rahima tana ta mitar wahalar tafiyar da zasu yi a ƙafa kafin isar su gidan . Da wani tasowar sabon yanayi a zuciyar Yakaka take bin unguwar da kallo , unguwar da ta zama tushe na hargitswar rayuwar ta da bata tsinci kome a ciki ba illa wahalhalu da tarin abubuwan ƙi , unguwar da suka sha gwagwarmaya a cikin ta ita da ƙanwar ta da ƙawarta Yagana ko ina yagana take a halin yanzu ? Wataƙila ita rayuwa tayi mata kyau , tayi aure ta fara ginin rayuwar 'ya'yan ta . tunaninta ya katse lokacin da Rahima ke cewa su gangara , Tana bin layin tana tuno da haɗuwar su da Doctor Hamza a bakin layin ana ruwan sama ,taimakon da yayi mata a ranar da ba domin shi ba da ta faɗa babbar kwatar taji mummunan ciwo ko ma ta rasa ranta , "Allah sarki yaya dakta , Ta furta hakan daga ƙasan ranta lokacin da suke miƙawa cikin layin . Daga nesa ta fara jiyo hargowar sa muryar sa a sama yana rantse-rantse , domin ta tabbatar da shi ɗin ne ? Tayi saurin ɗaga idonta ta ɗora a kan sa shi da wata matar da kallo guda tayi mata ta gane yanayinta na matan banza , Da sauri ta ɗauke kai tana ɗan jawo hijabinta gaba kaɗan , zuciyarta cike da fatan Allah ya rufe masa ido ya wuce bai ganta ba bare ya gane ta. cikin rashin sa'a hasken da take da shi ya riga ya ɗau hankalinsa kasancewar sa kawali idanun sa koyaushe akan wankakkiyar mace yake babu ruwansa da matsayinta na matar aure ko akasinta . Sun ƙaraso gaf da juna ya jaa ya tsaya , kafin ya ɗau salatin da Hajja ta ƙarasar masa , Sauri yayi ya zagaya ta sashin ta ya dogare , yana kallon fuskar ta da taƙi yadda su haɗa ido , Dariya ya kwashe da ita yana tafa hannuwan sa alamun mamaki yace , "Ahayye nanaye ke duniya mai abun mamaki ? Yanzu duniya da gaskiya Yaks kƴa ga Ɗanliti ki ɗauke ido ki kawar da kai ? Lalle Yaks kin zama kaza ci ki goge bakin ki , Ko da yake ai kome kika yi ba mamaki tunda baki da shayin kowa . Yakaka ta saci kallon Hajja wacce tayi saƙare tana bin Ɗanliti da kallon banza , " Ɗan-Ɗan liti ya kake ? " Ras nake Yaks . Yayi fari da ido kafin ya ɗora da "Ke kuma fa ? Ya na ganki haka da Bargo yaro-yaro kina yawo kadda dai kice min kin yi ƙarkon kifi , ? Kin fito daga ruwa kin faɗa wuta ? Yo ai kuwa da kin ɗibga asara a duniyar nan Yaks ace dai wai mace hamshaƙiya kamar ke kina yawo a ƙuɗunɗune cikin hirami yake ko hijabi ko jallabiya ? Bani sunan sa ɗaya . " Ubanka yake nace Ubanka yake shashasha , wofin wofiyo banzan banza , yau ga ɗa ya zama lalatatce bayan an kashe ragon suna , to Allah ya shirye ka , ke un-un Yakaka wuce muje . Hajja ta furta hakan tana huci tare da yiwa ɗanliti daƙuwa da hannuwanta duk biyu , ta ƙarasa zancen da fusgar hannun Yakaka , Buɗe baki Ɗanliti yayi da mamaki , ," Ke tsohuwa , ki kiyayeni ki kiyayen nace da zaki zo ki shiga cikin maganata dake nake ? Nace da ke nake ? Yo Allah na tuba ke a zamanin ki waye ya san irin tsiyar da kika shuka ta rawar banjo da kiɗan gurmi daga ke sai ɗan kanfai ?  Ko da yake wannan baƙin naki uwa shuni ba wani tasiri kika yi ba ko a wajen su garbati mai kalangu . , ",Na rantse kin ci darajar yaks domin ni na falle tsohuwa da marin da zai sa ta ga star abune mai sauƙi a wajena , gaba ki kiyaye kin ji na gaya miki . tsaki Hajja tayi suna barin wajen , " Allah ya shirya ka zindiƙi . Shima ya rama Hararar da tayi masa , " waye yake ta taki tsohuwar guzuma , Yaks Ki samu lokaci ki leƙo mu akwai labarai da hanyoyin arziki masu tarin yawa , af na manta na faɗa miki uwarɗakin fa bata da lafiya... Bai ƙarasa zance ba yayi shiru ganin sunyi nisa , " ji min tsohuwar nan zata yaɓan magana wai nine zindiƙi ? Tsohon ki ne dai zindiƙi aikin banza . **** Da sallama suka shiga gidan Amne , tana zaune kan barandar ta tana ƙunsa lalle a ƙafafunta da basa rabuwa da ƙunshi , Tayi mamakin ganin su saboda Rahima bata sanar  da ita zuwan nasu ba , ta tare su da fara'a tana yiwa baƙi barka da zuwa , idanunta da hankalinta baki ɗaya akan yakaka . Bayan sun gaisa ta dubi Rahima , " aina kika sake samo min mai kama da Rahima ta ? Da ace shekaru basu jaa dayawa ba zan iya cewa Rahima ta ce wannan ,   " dariya Rahima tayi , Amne baki gane ta ba ko ? Yakaka ce fa , 'yar gudun hijarar da suka zauna a gidan mu shekarun baya da akayi zaton ta rasu wajen haihuwa ? duk da ba wani jimawa tayi da yaran ba amma sunan su ya tsaya a ƙwaƙwalwar ta , " Yakaka ke ce ?   " ni ce Amne , " Alhamdulillah ashe Yakaka kina raye ? Ina kika tsaya tsawon lokacin nan ? Ina ƙanwar ki tare da 'yar ki ?   hannun ta ta ɗora akan na Amne da ta miƙo mata su , fuskar ta ɗauke da murmushin jin daɗin zallar ƙaunar da ta hango a idanun Amne ta matso kusa da ita , "Falmata su na America wai . Hajja tace , " Wai ne ma ?  ai ya wuce wai ., Amne bata tsananta tambayoyi ba ga Yakakar domin ta bata damar sakewa ,  Lallen da Amne take sawa ta karɓa , tare da cewa " kawo na sa miki Amne . tana murmushi ta miƙa mata 'yar robar da lallen ke ciki , ta shiga sanya mata sannu kan hankali , da sauri Rahima tace "Daman kin iya lalle ne Yakaka ? tana murmushi tace , " ko ban iya ba zan koya a ƙafar Amne . Hajja da Amne suka cigaba da hirar su , zuwa lokacin da Rahima tace , " Yauwa Amne ki nunawa Yakaka Hoton Khaalty Rahima da kike cewa suna kama Yakaka tana son ganin ta... "eh Amne ina son ganin Khaalty Rahima , Yakaka ta furta hakan cike da ɗoki .. Assalamu Alaikum masu karatu maza da mta , ina miƙo sakon gaisuwa ta tare da fatan alheri , ɗauke da yabawa bisa ga yadda kuke bin littafin nan cike da bani ƙwarin guiwa nagode ƙwarai da gaske Allah ya bar so da ƙauna ( sunan wani littafi 😂 ) sharhin ku a fejin da ya gabata ya min daɗi matuƙa da fatan za'a ɗore da haka ? . Ghost readers muna nan da ku , za'a ji kan mu watarana . 😡 Nagode .               [10/26, 11:28 PM] +234 706 503 6187: MAFARI ( Hargitsin Rayuwa ) Umm'muaz 37 Cike da zumuɗi Yakaka ta karɓi wani ƙaramin envelop ɗin da Rahima ta ɗauko mata daga ɗaki tana cewa " Yakaka ga hoton Khaaltƴ Rahima duba ki gani, ita ce takwarata ai ina kama da ita ko ?  . Da murmushi bayyane kan fuskar ta , ta zaro hoton bayan ta goge hannun ta da yake da ɗan danshin ruwan ƙunshi . Ƴar ƙaramar budurwa ce a jikin hoton na farko da baza ta wuce shekaru sha huɗu zuwa sha biyar ba , fara ƙal tamkar baturiya ,  ƙibabbiya 'yar dumur-mur  jikinta sanye da doguwar rigar iya ƙwauri mai guntun hannu irin shigar su ta shuwa ,kanta ba ɗankwali sai manyan kitson guru da aka mata gwammon sa a ƙeya , " wai Masha Allah Rahima mai sunanki ta fiki kyau gaskiya , Ta furta tana 'yar dariya kafin ta zame hoton na bayan sa ya bayyana da bai kai wancen a tsufa ba domin a wannan ta ƙara girma ta zama budurwa da a lokacin zata iya kaiwa shekaru sha bakwai , da alama a makaranta ta ɗau hoton ganin jikinta sanye da uniform , Tsam , tayi tana ƙurewa cikakkiyar fuskar ta kallo da take dariya ,  tamkar dai tana rikiɗe mata zuwa fuskar da tayiwa sani na haƙiƙa , "fuskar wa ? Ta tambayi kan ta da kan ta . "Fuskar maman mu ," babu shakka dariyar ta da zubin haƙoranta irin na maman mu ne , sai dai maman mu bata da jiki da kyaun wannan mai kama da turawan, Tunanin ta ya katse lokacin da ta tsinkayi muryar Amne wacce ita ma ta kafe ta da ido tana nazarin yanayin da take hangowa a tare da ita , " Yakaka ko kin san ƙanwata Rahima a wani waje ne ? Kallon Amne tayi kamar zata ce wani abu sai kuma tayi ɗan yaƙe , tare da girgiza kanta lokacin da take ƙoƙarin mayar da hotunan cikin gidan su , " A ah Ban san ta ba Amne ," "Allah sarki , Rahima kenan ƙanwata da muke uwa ɗaya uba ɗaya jal a duniya , Yaa Allah ka san halin da na wanzu cikin sa tsawon shekarun nan akan rashin Rahima , Allah ka dawo min da Rahimatullah , ka sa muna da rabon sake ganawa a duniya . "Amin Amne , suka amsa mata su duka fuskokin su na bayyana alhini , musamman Yakaka wacce ta shiga wani irin hali na ruɗani da ganin hoton khaalty Rahima ya jaza mata  . Ƙwarai fuskar ta tsaya mata a zuci da cikin tunaninta , Babu wadatar nutsuwa na sosai a tare da ita suka ƙarasa yinin su zuwa gefen La'asar suka kama hanyar komawa gida , Rahima ta dubi Yakaka bayan mai adai-daita ya sauƙe su a daf da ƙofar gida , "Yakaka ya naga duk kin yi wani iri , akwai damuwa ne ? Kafin mu fita a gida ba haka kike ba , Kafin Yakaka ta amsa Hajja tayi charaf ta amshe zance , "Ahaf zai wuce batun wannan ɗan  banzan , ɗan hamsin yake ko ɗan daudu ? Idan har kika ce ƴar huɗubar wofin nan da ya wassafa miki zaki ɗauka ki aza a rai to kuwa kin kama kumfar teku , domin wannan da kike ganin sa rabon sa da alasambarka tun kwanansa bakwai ran suna , babu Alheri a tare da shi ko na aninin kobo  atoh . A ɗan kaikaice Yakaka ta dubi Hajja zata yi magana , aka buɗo babbar ƙofar gidan , Doctor Hamza ya turo kan motar sa , kallo guda ya yiwa gefen da Yakaka take ya ɗauke kan sa , Da sauri Yakaka ta wuce tana gyara zaman hijabinta , ta bar Rahima da Hajja suna gaisawa da shi , inda yake tambayar su daga ina suke ?? Suka sanar da shi daga gidan Amne suke , sosai ya ji daɗi tare da tambayar su yadda suka baro ta ? Suka amsa masa da tana lafiya ƙalau , Daga haka ya wuce yana satar kallon madubin motar sa inda ya hango Bayan Yakaka tana tafiyar ta a hankali dogon hijabin jikinta da yake kusan taɓa ƙasa bai boye salon takun tafiyar ta irin na barewa ba , Ɗauke kai yayi lokacin da yake dai-daita kan motar sa ya hau titi ya cilla zuciyar sa cike da zullumin tunani kan inda ya nufa , Kai tsaye ya tasamma unguwar da aka bashi tabbacin anan gidan da matar nan da yake zaton innar sa ce take aiki , duk kuwa da cewa duk cikin binciken da ya gabatar na tsawon satika biyu bai samu wani abu da zai bashi tabbacin cewa ita ce ko ba ita bace ?  Amsa guda ɗaya ta tabbata a gare shi , shine matar kurma ce kuma ƴar gudun hijira ce daga yankin Bama , da take rayuwa tsakanin gidajen masu kuɗi tana yin aikace-aikace da ita da tilon ɗan ta mai kimanin shekaru takwas . Yana shiga unguwar ya bi kwatacen gidan da aka ce tana aiki da su , ya tsaya daga bakin babbar ƙofar gidan ya nemi iznin shiga daga dattijon dake gadin gidan , Ganin sa da dattijon yayi cike da haiba da alamun wadata ya sa shi yin tunanin ko ire-iren mutanen da suke mu'amala ne da masu gidan , dan haka kai tsaye yayi masa iznin shiga da motar sa harabar gidan , Bayan ya fito daga motar sa ya miƙawa dattijon hannu suka yi musabaha , "Baba ina neman Mamar Bulama ne ance nan gidan take aiki ? "To oho Kurma Mamar Bulama ƙwarai kuwa nan take aiki idan ka miƙe wannan yar hanyar ka ƙure sashin su yana nan daga hannun ka na dama nan za ka ga wata ƙaramar ƙofa , " toh sannu Baba nagode sosai . Har ya fara taku , sai kuma dattijon da yake bin bayan sa da kallo ya dakatar da shi , " Amm bawan Allah nace ko dai lafiya kake..   Wata bangazar da ɗan yaron da ya kwaso da gudu yana gara gare-garen sa ya yiwa dattijon shi ya hana shi ƙarasa zancen sa yayi taga-taga , hular kan sa ta faɗo , Da sauri Doctor Hamza ya kama masa yana masa sannu , A fusace ya ɗago kan sa , " wannan akwai hatsabibin yaro , Bulama , Bulama , ai ko dan kai nayi fatan a kori uwarka daga gidan nan kafin ka kassara ni ko ma ka kar ni baki ɗaya ,  " wallahi bawan Allah a rana Bulama bai kuskureni ba ya kuskureni sau takwas , ka ga nan " ya nuna masa dai-dai muƙa-mukin sa da ya ɗan kunburo  " jiya-jiyan nan iwar haka Bulama ya auno min jifan wani mulmulelen dungur , haba me ake da giggiwa irin ta 'ya'yan sansanin gudun hijira , Da tausayawa Doctor Hamza yake ba shi haƙuri tare da yi masa sannu , kafin ya sanya hannu cikin aljihunsa ya zaro gudar dubu ɗaya ya miƙa masa , "Sannu Baba ga wannan ka saya manzafi ka shafa a wajen ka kuma dunga sa ruwan ɗumi , Da sauri dattijon ya wafci kuɗin yana ƴar dariya , "Kai to madalla , Madalla bawan Allah nagode , ai ka gane kwatancen da nayi maka ko ? Ko na raka ka ne ? "Nagane Baba zan shiga da kaina , Kai tsaye ya doshi sashin , a ƙofar ya tsaya yayi sallama bai ji an amsa ba , baki uku yana sallama ba amsa , Cike da nutsuwa ya tura ƙofar da take ta ƙarfe ya shiga faffaɗan filin da yake ɗauke da wasu ɗakuna uku daga kan wata yar baranda , Yawata idanun sa yayi a filin wajen , daga gefe ya hangon ta a zaune , tana soka allura da zare a jikin hular da take hannunta tana ɗinkawa , Yayi mata kallon mintuna biyu masu kyau kafin ya fara taku yana kusantar ta , zuciyar sa cike da yaƙini kan kasancewar ta innar sa , Kamar daga sama ya faɗo haka ya gan shi tsil a tsaye a gaban shi yayi banga-banga ya riƙe kunkumi , Duban sa ya mayar kan sa yaro ne da bai wuce shekaru takwas ba fari kal da shi irin mamar sa , launin idanun sa yayi masa yanayi sosai da na wata da ya sani da a lokacin baida damar zurfafa tunanin ganota, Girar sa ya ɗaga yana kallon yadda yaron ya ƙanƙance ido yana wani kumburi kamar mai shirin dambace sa'an sa , ya gane shi sarai yaron nan ne dai da ya bangaje dattijon nan a waje , Murmushi yayi tare da miƙa masa hannu , "Salamu Alaikum abokina , ni sunana Dr .   Tsuke baki ya sake yi , kafin ya amsa cikin dakiya " Ni kuma sunana Bulama , waye kake nema ?  Wancen mamata ce sunan ta Mamar Bulama , nan wajen mu ne masu aiki ,  can babbar ƙofar can nan ne wajen ku 'yan gayu , Mayar da hannun sa aljihu yayi ya gyara tsayuwa yana murmushi tare da mayar da hankalin sa kan yaron domin sosai yanayin wayon sa da tsaurin idon sa ya burge shi , " wajen Mamata nima na zo ba wajen yan gayu ba ,   Da sauri Bulama ya katse shi "waye mamar ka to ? Da baki Doctor hamza ya cuna masa Mamar Bulama da take nesa da su ta duƙufa ɗinkin ta babu alamun ta san da tsayuwar su a wajen. ' Ga mama ta can , Da sauri ya waiga ya dubi Mamar sa , sai kuma ya dawo da ganin sa kan Doctor Hamza . " Mamata ce Mamar ka ? Ya furta hakan yana bin shi da kallon mamaki daga sama har ƙasa , "unhun , Doctor Hamza ya amsa masa yana ɗaga kai alamun tabbatarwa Da gudu ya juya wajen Mamar sa yana dariya ,   Da murmushi ya bi bayansa zuwa inda take  Yana zuwa faɗawa yayi a kanta , zabura tayi da ya sa allurar da take ɗinki da ita ta soki hannun ta , Dungure Bulama tayi tana harararsa . Bata lura da kasancewar sa a wajen ba , sai da ya kamo hannunta da ta riƙe tana duba wajen da allura ta soke ta da har yake jini , Da firgici take kallon sa da ya sa ɗan hankici yana naɗe mata hannun , sannan yana ce da ita , "A iya sanina Uwa bata gudun ɗan ta kome muni ko tsananin Lamari , a matsayin da muka ajiye juna tun farkon-fari mun fi shaƙiƙan abokai kusanci , ina zaton kin manta da kika ce ke zaki fara rakani taɗi wajen budurwata ranar da zan fara tsayawa da ita , sai kuma ga shi shekaru sun tafi sun yi nisa cikin wani irin bauɗaɗɗan lamari marar daɗi , da har ɗan nan naki yayi aure baki sani ba , ba kuma kya son sani , Ya ɗago kan sa bayan ya gama naɗe mata hannun , ya kalli ƙwarar idanun ta da suke sake bayyana masa tare da tabbatar masa ita ɗin ce dai , Da wani irin yanayi yace , "khaalty nasan kina ji na , kin kuma gane ni , idan baza ki magantu domi na ba , ki magantu dan Amne Amina , ki dubi girman Allah ki waiwayi 'yar uwarki , ki koma mata ko rayuwar mu zata dai-daita gaba ɗaya , "kar a tuno da kome da ya riga ya faru  ya wuce , yanzu lokaci ne yayi na gyaruwar kome , Hawayen da suke sauƙa a idanunta ne suka ɗigo akan bayan hannun sa Hannun sa ɗaya ya kai da nufin goge mata ,    Bulama wanda idanun sa suka kaɗa suka yi jaa yana daf da fashewa da kukan shima , ya ture hannun Hamza , ya sa 'yan tafukansa biyu ya share mata hawayen , kafin ya waigo gareshi , " Kai ba yaron ta bane tunda ga shi ka sa ta kuka ka tashi ka bar gurin mu , " ka fita Ya ce yana tura Doctor Hamza Doctor hamza ya miƙe a hankali ganin taƙi cewa kome ga kuma hayaniyar Bulama da take ƙara damun sa . Yayi taku biyu yaji tayi magana da sautin da baya fita mai kyau irin ns bebaye , Juyowa yayi sai ya ga ta miƙo masa hannuwanta irin yadda take yi masa tun suna yara , Da murmushi a fuskar sa ya koma yana sassarfa ya harɗe yatsun sa cikin nata da zuwa lokacin kuka take haiƙan , "la bas , ki daina kuka khaalty , Yake cewa ga ita da sigar rarrashi . Hawayen ta ta goge Bulama yana taya ta kafin ta sunkuya ta share rairayin da yake ƙasa ta rubuta masa da yaren su ,     kayf hal 'ukhti  ? (Ina yar uwa ta ?)  kayf tamakanat min aleaysh bidun ily?  ( yaya tayi rayuwa bayana ? )   Kafin ya amsa mata ta sake rubuta masa wata kalma " aftaqadaha kathirana , ( nayi kewar ta sosai ) A takaice ya bata labarin Amnee da mafi yawa yafi karkata ga halin damuwar da take ciki akan rashinta , ya ɗora da sanar da ita rabuwar auren iyayen sa , da haifar da ruɗani tare da ƙaruwar zubar hawayen ta , Ƙarshe ya roƙi da ta zo ya kai ta wajen 'yar uwar ta . Nan ya ga sabon ɓacin rai akan fuskar ta kafin ta tirje ta nuna ƙin amincewarta da batun , Duk yadda yake zaton lamarin zai kasance ya wuce haka , domin kuwa a ƙarshe ta sanar da shi muddin ya matsa kan batun komawar ta gida zata bar inda ya sani ta sake maɓoya ita baza ta taɓa komawa gida ba  . Rochester New York Cikin kwanakin da suka biyo bayan zuwan Falmata asibiti tare da fara shan maganin ta , sosai aka samu cigaba ga lafiyar idanun ta inda cikin satin ta na biyu da fara shan maganin ya zamana tana iya ganin alamun haske fayau amma bata ganin hoto , hasken ma wasu lokutan yana zama babu ,a wasu lokutan kuma yana mata yawa sosai ta yadda har take gagara buɗe idon , Hakan ya sa da ta yiwa likitan ƙorafi sai ya bata shawarar ta nemi tabarau da ake amfani da su wajen rage ƙarfin hasken rana , watau tabarau masu duhun launi , bayan haka kuma ya sake shawartar su akan amfani da sandar makafi , ( white cane ) Domin zai taimaka mata wajen gudanar da al'amuranta na yau da kullum a sabbin wuraren da bata kai ga sani ba , zai kuma bata kariya tare da zama garkuwar a gareta . Dan haka Biyamuradi ya tafi kanti da kan sa ya zaɓo mata tabarau masu kyaun suffa na mata , tare da sayo mata sanduna har guda biyu . Falmata wacce tun ranar da ta saurari hirar Biyamuradi da Maimounatu duk ta zama wata iri , damuwa tayi mata yawa sannan 'yar sakewar da ta fara yi da shi ma duk ta bi ta daina ta koma takura kan ta kamar farkon auren su . A hankali ta lura da yawan yin waya da mata biyu da yake yi daga barandar gidan ta waje , ta gane su biyu ne ta yadda daga ya gama waya da ɗayar yake ƙiran ɗayar , sai dai ko kusa taƙi yadda ta sake saurarar hirar sa da ta lura shima bai son ta ji tunda fita yake yi idan zai yi wayar sannan ko Mama bai yadda ta bi shi . A ɓangaren Biyamuradi shima shirun Falmata tare da damuwar da take ciki ya fara damunsa , sai kaffa-kaffa yake yi da ita yana ta bin hanyoyin ganin ya dawo mata da walwalarta kamar farkon zuwan su , A yau ma yana zaune tare da su a falo Mama tana wasan ta a gefe da tilin kayan wasan da ya sayo mata su tari guda tarkace iri-iri . Wayar sa tayi ƙara alamun shigowar ƙira , hannun sa da yake dafe da kan sa da ke ɗan masa ciwo sama-sama ya janye daga kan shi tare da yunƙurawa ya zauna sosai ya ɗau wayar sa , Ganin wanda yake ƙiran nasa ya sa shi tattaro duk wata nutsuwar sa , " Assalamu Alaikum Maimartaba barka da war haka da fatan alheri . Daga can Maimartaba ya amsa masa , suka gaisa , kafin ya jefo masa tambaya da ta so ruɗa shi da farko " Youssoufa wake tare da kai nan ƙasar Amurka ? Kacce bisa ga aiki ka tahou nan kou ? Satar kallon Falmata yayi wacce take zaune daga gefe a ƙasa , Sai ya miƙe ya fita Bata ganin sa amma taji takun barin sa wajen , ajiyar zuciya ta sauƙe tana jin damuwar ta na sabunta , " wayar zai je yi da su ,    Ta aiyana haka a cikin ranta . "Ranka ya daɗe bissa aiki na zou nan kouma tare mukke da abokan aiki na kamar yadda na faɗi tun farko , Daga ɓangaren Maimartaba sarki Abdoul-Azizou yayi shiru yana nazari , kafin ya amsa " Madalla Allah shi taimaka yaushe kake dawouwa ? Cike da jin daɗi Youssouf ya amsa da "ƙasa da watanni huɗu ko biyar ranka shi daɗe , "Allah shi dawo da ku lafiya , ka tsayar da gaskiya cikin dukkanin lamuran ka , sannan ka tsananta addu'a . Ya amsa da "  to nagode sosai Ranka shi daɗe . Suka yi sallama , ajiyar zuciya ya sauƙe yana nazarin Kalmomin Maimartaba kamar akwai dalilin yin su ,musamman ma tambayar da yayi masa a farko. Nisawa yayi kana ya dubi fuskar wayar sa ya ga agogo ƙarfe uku na yamma ta kusa , can gida Niger yanzu tara na dare ne kenan Maimartaba yana sashin sa suka yi waya ? Bai tare da hajiya Umma domin da zai haɗa su su gaisa . Kawar da tunanin yayi ta hanyar lalubo layin wayar maimounatu bata jima tana ƙara ba ta ɗaga cike da salonta na ƙwarƙwasa wanda yake da tasiri sosai agare shi , Yana nan a tsaye a wajen ya kwashi fiye da rabin awa yana hirar da ita ke tsawaita masu ita ta hanyar amfani da daɗaɗan kalmomin ta , Da suke ɗumama masa zuciya da jiki daga barin jin matsanancin sanyin da ke farfajiyar wajen . Da kyar suka rabu kafin ya ƙira Siyama sama-sama suka yi hirar da yafi karkatata ga tambayar lamuran da suka shafi 'yar sa ita kuma siyama tafi damuwa da lafiyar sa tare da lamuran sa na yau da kullum . Bayan sun gama wayar ya maida ta aljihu ya ɗaga kai yana kallon yadda garin yake lulluɓe da tsananin sanyi . juyawa yayi ya koma ciki nan ya tarar da irin ɓarnar da Mama take yi ta gan-gama wuta sosai a ɗan wajen hura wuta har wutar ta fito waje tana gaf da kama 'yan ƙananun kayan wasan ta da ta riga ta jefa wasu cikin wutar da hakan ya sa wutar ƙara ruruwa sosai . " Mama me kike haka ? Yace da maɗaukakin sauti da ya sa daga Mama har ita kan ta Falmata suka firgita , da sauri Falmata ta yunƙura tana laluben Mama cikin tambayar me take yi ? Biyamuradi da takaicin yadda Falmata take yin jugum kamar mutum-mutumi ya fara isar sa ya dube ta a fusace , "Tayaya zaki iya sanin me take yi bayan baki da wani aiki sai tunanin wofi tamkar kin fi kowa damuwa a duniya , Saitin da yake Falmata ta maida ganin ta da kalamansa suka tunzuro ta ƙari da takaicin hirar da yake da matan banza a zaton ta , Muryar ta babu ƙarfi sosai tace , " ai ni miskiniya ce marar ido da bata wuce mabaraciya ba ,  da zai fi dacewa a cikin matan da kake taɗi da su kullum ka auri ɗaya da zata dunga kula da gida sosai , Chak ya tsaya daga tattara kayan wasan Mama , ya maida ganin sa kanta , yanzu ya samu ƙarin haske akan yadda ta sauya yake ganinta koyaushe cikin fushi da ɓacin rai ashe kishi ne ke cin ran ta , Murmushi yayi ya bar abunda yake tare da dawowa gefen ta ya zauna ya riƙo hannun ta , tausasa muryar sa yayi yana me tsare ta da ido yace , " Fatima ki saurareni , ki ji abunda zan faɗa miki a yanzou domin shi zai amfanar mouna ni da ke , matan da kike ji ina waya da su su biyu ba matan banza bane Matana ne su ma kamar yadda kike Matata . Kamar ya caka mata wuƙa sai ta zame hannun ta daga cikin nasa , bakin na motsi a hankali , Bai kula da yanayin ta ba saboda ya shirya faɗa mata gaskiya a yanzu , ya sake riƙo hannun ta tare da cigaba da magana , " Fatima kiyi haƙuri amma yau zani faɗi miki doukkanin haƙiƙanin gaskiya bisa kaina . Bai jira amsar ta ba ya shiga bata labarin ko shi wanene tiryan-tiryan , tundaga sunan sa na gaskiya,  kasancewar sa ɗan sarki , aikin sa zuwan sa Nigeria auren sa da matan sa , abu guda ya ɓoye mata haƙiƙanin dangantakar sa da Yakaka . Tamkar a mafarki haka Falmata ta tsincin wasu kalmomin nasa , cikin wani irin yanayi da ta gaza tantance wanne iri ne , muryar ta can ƙasan maƙoshi , tace da shi " Duk cikin labarin da ka bani baka faɗa min lokacin da kuka yi aure da 'yar uwata ba ? Mukut !  Youssouf ya haɗiye busasshen yawu tambayar ta zo masa a bazata ta yi masa dirar mikiya bai kuma shirya amsar bata ba a yanzu , " Fatima zan faɗi miki wannan labarin a gaba cikin lokaci na mussaman ba yanzu ba , Cikin rashin yarda da ya mamaye tunanin ta ta fara girgiza kai , " a ah yanzu nake so ka faɗa min muddin kana so na yarda da duk labarin da ka bani yanzu , zaro ido yayi yana duban fuskar ta da ƙwayar idanun ta da suke cike taf da rikici da tashin hankali , Ya ɗan ɗaga sauti yana murza yatsun ta dake cikin hannun sa , " Fatima ki nutsu nace zan faɗa miki watarana a gaba , Warce hannunta tayi da ƙarfi daga cikin nasa ta matsa daga kusa da shi cikin ɗaga sauti ita ma ta ce masa " Ba gaskiya bane muddin baka faɗa min yadda kuka yi aure da Yakaka ba kai ba kaine Baban Mama ba ƙarya kake min ,   Tsawar da ya daka mata tare da buga teburin gaban su shi yasa Mama fashewa da kuka da gudu tayi jikin Falmata ,    wannan karon ya kaurara murya da wani irin amo da bata taɓa jin sa da irin ta ba cikin sigar gargaɗi yace mata ,   " Fatima ki min shiru , ki min shiru nace kar ki sake cewa ƙala , Fuskar sa tayi jazir , jijiyoyin kansa sun fito ruɗu-rudu , baki ɗayan jikin sa yana rawa , ɓacin rai sosai ya sauƙo masa , zafin zuciyar sa irin ta soji ta hayyaƙo , A zabari ya miƙe ya shiga ɗaki , yayi tsaye hannun sa a dunƙule , ya rasa me yake yi masa daɗi wani irin ɓacin rai me tafe da tsoro-tsoro da a lokacin ya rasa tsoron meye ? Shine yake cin sa , Jibgegiyar rigar sanyin sa iya guiwa dake ajiye a gefen gado ya ɗauka ya rufa akan kayan sanyin da daman suke jikin sa ya fito daga ɗakin , Satar kallon inda suke yayi ya ga Falmatan tayi baya da kanta ta kwantar akan kujerar Mama kuma tana maƙale a jikinta tana kallon sa da raunanan idanun ta , Tausayin 'yar sa ya kawo masa , da hannu ya yafice ta , da sauri ta sauƙa tayi wajen sa , Ɗaukar ta yayi ya koma cikin ɗakin ita ma ya ƙara mata rigar sanyi tare da sauya mata hular da tafi ta kan ta nawi ya sungume ta suka fito falon ba tare da ya dubi sashin da Falmata take ba ya nufi ƙofar fita , Mama da idanun ta ke kan Mamar ta cikin siririyar Muryar ta tace "Papa ma.... 'shit Yace mata yana ɗora yatsan sa manuni akan bakin ta , shiru tayi tana kallon sa suka ƙarasa ficewa daga gidan ya ja ƙofar Ƙarar rufuwar ƙofar ya zo tare da zubowar kauraran hawayen ta , da duk motsin su daman yana kunnen ta , Kuka ta fashe da shi mai sauti tare da jin wani sabon tashin hankali har ta rasa takamaimai da wanne zata ji ? Shin laifi ne dan ta tambaye shi game da yayar ta ? A sautin sa ta tsinkayo tashin hankalin da yake tafe da rashin gaskiya shin meye yake boye mata bayan wanda a yau ya bayyana mata da ta haƙiƙance ta kuma yarda ɗari cikin ɗari gaskiyar sa ya feɗe mata da ita kuma ganin wannan damar ne ya sa tayi amfani da ita wajen shigo masa da tambayar da ta kwashi shekaru tana cinta a rai , " Yaushe suka yi aure shi da Yakaka alhalin ita bata san lokacin ba ?? Tana share hawaye wasu na zubowa , "Wai ashe daman har yana da mata biyu ita bata sani ba ?ashe mijin su ne su uku ? Tausayin kanta ta ji ya kawo mata , tabbas ita ba kome bace a wajen sa face wacce ya taimaka ya aure ta sanadin 'yar yayar ta , ba kuma zata taɓa zama kome a wajen sa  ba , 'idan kuwa haka ne dole tayi haƙuri ta haɗiye kome ta kuma bar kome domin ta cigaba da zama a ƙarƙashin sa tare da Mama , a zahiri yake ai shi yafi ƙarfin auren ta , wacece ita ? Miskiniyar ɗiyar talakawa 'yar gudun hijira ? Babu shakka bakin rijiya ba gurin wasan makaho bane , Ya zama dole ta bashi haƙuri idan ya dawo ta kuma alƙawarta cikin ran ta baza ta sake yi masa batun Yakaka ba . Ta ɗau lokaci a haka cikin kukan zuci da damuwa , kafin ta kintata tayi sallar la'asar da take da tabbacin lokacin ta ya shigo , A ƙasa inda tayi sallar ta cigaba da zama tunaninnika sun mata yawa , ta ƙagauta ƙwarai ta ji motsin shigowar sa ta bashi haƙuri , Daƙiƙoki suka dunga hanzarin wucewa suna zama mintoci har suka ɗebi awannin da Falmata ta ji su tamkar sati guda tayi tayi a zaune , Ta tashi ta tsaya yafi a ƙirga ta matsa jikin ƙofa ta laluba , ta kasa kunne ko zata ji motsin su , har dai ta tabbatar sun yi nisa da ita sosai , Wani irin mummunan tashin hankali ne ya dirar mata sakamakon tunanin da ya gitta ƙwaƙwalwar ta kan cewa ya ɗauke ɗiyar sa sun tafi sun bar mata gidan , ya sauya muhalli sun yi nesa da ita har abada , ya tafi ya bar ta a uwa duniya ƙasar da bata san kowa ba ko yaren su bata ji , Wannan karon kukan da ta fashe da shi tafe yake da amon matsanancin tsoro da ruɗewa , Da gudu ta taka tayi nufin fita sai dai karon da ta ci da kujera yasa tayi baya  cikin sa'a ta zauna daɓas akan kujerar kusa da ita , Ta sake ajiye hannu da zummar miƙewa hannunta taji ya sauƙa akan sandar ta , cikin sauri ta laluba ta ɗau sandar , ta kama hanya fita daga gidan tare da taimakon sandar hannunta, Bata damu da ta sake ɗora wata rigar sanyi ba illa ta jikinta da take iya guiwar ta sai kuma siririn siket da hular sanyi a kanta ta fice a gidan ba tare da ta san ina ta dosa ba , Tsananin sanyin da ya ratsa ƙasusuwan ta lokacin da ta fito waje bai sa ba ta koma illa tafiya da ta cigaba da yi tana laluben hanya da sanda , Unguwar da suke shal babu kowa sai tsilla-tsilla motoci ke wucewa haske ya wadaci ko'ina da taimakon fitulun gefen hanya duk kuwa da duhun dare da ya fara mamayar sararin sama. Tayi tafiya mai nisa lokacin da tsoro ya gama cin galaba akan ta nadamar fitowar ta ya ziyarce ta , Matsanancin sanyin da ya fara cin ƙarfin ta sakamakon dusar ƙanƙarar da ya fara sauƙa ya sa ta gaza ci gaba da tafiya gaba ɗaya ji take kamar jinin jikinta ya daskare , Durƙushewa tayi a wajen da bata da masaniyar ina ne ?tana jin yadda sanyin wajen da ta zauna yake ratso jikin kayanta yana daskarar da duk wani ruwa na jikinta , Idanunta da hancinta suna tsiyaya ta dunƙule jikinta waje guda tana karkarwa , A cikin ran ta ta haƙiƙance rayuwar ta  ta zo gangara , ashe ita kuma irin tata sanadin mutuwar kenan sanyi  ? **** Biyamuradi Youssouf tunda ya fita saɓe da Mama , yayi ɗan tattaki cike da rashin sani takamaimai ina zasu ?? Ya zaɓi ya fita ne saboda yana da yaƙini zuciyar sa ba zata jure ganin fushin ta ba , da shi kuma a wannan gaɓar bai yarda yayi wani yunƙurin ds zsi fallasa halin da zuciyar sa ke ciki ba a kan ta bai so ta gano lagon sa tunda wuri haka , Cigaba yayi da tafiya har ya cimma babban titi , nan ya hango wani shagon sayar da coffee , Bayan ya ƙarba musu coffee me zafi ya zaunar da Mama a kujerar da ke fuskantar ta shi , Juya ɗan chokalin hannun sa yake yi ya gagara shan coffee ɗin , damuwa tayi masa ƙawanya duk wata walwalarsa ta kau , Ko kusa ba zai iya duban ta ya fayyace mata lamuran da suka auku tsakanin sa da 'yar uwar ta ba , yana jin kunya , yana kuma tsoro . Meyasa ta kasa fahimtar barin abunda ya riga ya wuce a muhallin shuɗaɗɗan lamari shi yafi alheri fiye da tone-tone . ? Duban sa ya kai ga Mama wacce tayi shiru ta lanƙwasa kai fuskar ta bayyane da damuwa , Tausayin ta ya ji domin ya san damuwar ta ta samo asali ne ga abunda ya faru tsakanin sa da Falmata , da shima zuwa yanzu nadamar ihun da yayi mata yake yi , Bai yi hakan da wata manufa ba illa ruɗanin da ya tsinci kan sa a ciki da ya sa bashi da wata hanyar daƙile yunƙurin ta tare da kawo ƙarshen maganar idan ba ta hakan ba . Tashi yayi ya zagaya ya ɗauki Mama suka fito daga Coffee Home ɗin ba tare da ya sha coffee da ya saya ba , Sake nusawa yayi bakin titi yana tafe sannu kan hankali har ya tadda ɗan wani killacaccen wajen yin sallah , nan yayi sallar la'asar tare da Mama a gefen sa  , Bayan ya idar hankalin sa ya kai kan wani fili gaban wasu gidaje da matasa da yara suka taru suna wasan ƴar zamiya akan dusar ƙanƙara Tobogganing , kama hannun Mama yayi suka ƙarasa wajen , Ya zauna daga gefe kan kujerar gefen hanya tare da ɗaura Mama a cinyar sa , Sosai wasan ya ɗau hankalin Mama ganin yara ƙanana sa'o'in ta nata faɗuwa da tashi cikin dusar ƙanƙara , nan take ta shagala da kallon su har tana taya su dariya idan wasun su sun faɗi , Ganin walwalar Mama ya bashi damar zurfafa a tunani , sashi guda na ran sa na shawartar sa akan idan ya koma gida ya faɗa mata gaskiya ksn abunda take son sani , yayin da sashi mafi rinjaye ke ƙwabar sa tare da tsoratar da shi abunda faɗa mata gaskiyar zai iya haifarwa , Abunda ya haƙiƙancewa ba zai iya jurar fushin ta da damuwar ta ba domin kusa take sosai da ruhin sa , Bai ankara ba har duhun dare ya fara shigowa , dan haka ya sake komawa wajen da yayi sallah , ya sallaci Magarib  ,  Yana idarwa ya kamo hanyar gida bayan ya saɓa Mama a bayan sa da tayi laushi tuɓus , Ta gaban manyan shagunan sayar da kayan ƙele-ƙele na mata ya zo wucewa , idanun sa suka kai kan wata 'yar kyakkyawar sarƙa da take ɗaukar ido tare da taimakon hasken lantarki da ya haske cikin gilashin da sarƙar take . Murmushi yayi lokacin da idanun sa suka hasko masa sarƙar a cikakken wuyan Falmata , Da hanzari ya shiga shagon ya sayi  sarƙar da take ta farin zinare ƙirar ƙasar Amurka suka zare kuɗin su ta katin sa tare da zura masa akwatin sarkar cikin 'yar jakar da take ɗauke da tambarin Manns jewelry . Cike da fargaban halin da zai riske ta ciki ya nufo gidan , zuciyar sa na aiyana masa wataƙila tayi ta kuka ,?wataƙila kuma ran ta ya sake ɓaci da shi, koma menene zai bata haƙuri ys rarrashe ta ta bar maganar nan , Da Sallama ya tura ƙofar gidan ya shiga , Shiru ya ji bata amsa ba , Ya lalubi wutar falon ya kunna , Idanun sa akan ɗan wajen kunna witar ɗumama ɗakin da har wutar ta mutu , hakan ya sa ɗakin ya ɗau sanyi cikin ran sa babu daɗi  , Ya zaunar da Mama akan kujera , yayi tsaye yana saƙe-saƙe , jikinsa gaba ɗaya yayi sanyi da barin ta da yayi ita ɗaya , Takawa yayi ya ƙarasa bakin ƙofar ɗakin ya ɗan ƙwanƙwasa , " Fatima , mun dawo Ya furta haka da sauƙaƙar murya , Shiru ya sake ji babu alamun motsi , Sai ya murɗa hannun ƙofar ya shiga ɗakin , cikin 'yan daƙiƙai ya fahimci bata ɗakin , da sauri juyo , kai tsaye ya leƙa cikin ɗaya ɗakin , babu alamarta Tamkar an safure shi haka ya dunga bin kowanne lungu da saƙo na gidan yana neman ta tare da ƙira sunan ta , A ƙarshe ya hiƙanƙancewa kansa tabbas bata gidan , ta fita ne ? Ko an sace ta ? Shikenan shi kam ya shiga ukun sa , ta shi kuma ta same shi . Da gudu ya sunkuci Mama ya fito , dusar ƙanƙara na sauƙa a kan su yayi tirus a harabar wajen , ina zai fara nufa neman ta ? Wa zai dosa ya tambaya akan ta ? Gidan da yake maƙwaftan na su ya nufa da sauri ya danna musu ƙararawar neman iznin shiga gidan , Zuciyar sa na ayyana masa wataƙila ta shiga gidan , Tunanin sa ya katse lokacin da aka buɗo ƙofar wani mutum magidanci yayi tsaye yana kallon sa , Da harshen turanci ya gabatar masa da kan sa a gurguje kafin ya ɗora masa tambaya kan ko matar sa ta shigo gidan su ? Da harshen larabci mutumin ya miƙa tambayar ga matarsa da take daga bayansa a tsaye , Nan suka tabbatar masa da babu wacce ta shigo musu , Har ya juya sai kuma ya dawo , Rokon su yayi akan su taimaka su riƙe masa 'yar sa zai je neman matar sa , Basu musa ba suka karɓi Mama da tayi rau-rau da ido tana shirin kuka ganin Babanta zai tafi ya bar ta hannun waɗanda bata kai ga sanin su ba , Bai kula ba ya juya da sassarfa mai haɗe da gudu ya kama doguwar hanyar da tayi cikin unguwar sosai yana tafe yana dube-dube da waige-waige , hankalinsa yayi ƙololuwar tashi , maƙogoran sa ya bushe , idanun sa har raɗaɗi suke yi masa , "Yaa Allah Fatima ina kike ? Yaya za ki min hakka Fatima , ? Meyasa kika fita ? Ya furta hakan muryarsa na karkarwa , bayan hannun sa ya sa ya goge fuskar sa da iskar dusar ƙanƙara ta watso masa , Ganin har ya kusan ƙure unguwar bai gan ta ba ya sa shi komowa baya , yana cigaba da neman ta , addu'o'i iri-iri yake yi , Zai iya cewa tunda yake bai taɓa shiga tashin hankali irin na tsuƙin lokacin nan ba , bai taɓa sanin ita wata kadara ce mai maɗaukakiyar daraja a wajen sa ba sai a wannan gaɓar da yake gaf da rasa ta , bazai yafewa mummunar zuciyar sa ba idan har wani abun cutarwa ya same ta , Sakin hanya yayi ya nufi wata doguwar hanyar da tayi gefe a tsakankanin dusar ƙanƙara Fatima , Fatima , Fatima Yake ƙwala ƙiran sunan ta , Ya ƙure hanyar bai ko ga alamun sawun ta ba sai zunzurutun sanyin a yake ratsa sa , Dawowa yayi da baya ya sake kama wata hanyar ta daban nan ma yana tafe yana kiran sunan ta , Durƙushewa yayi a gefen hanya yana jin tamkar ya ƙwala ihu ko ya ji sauƙin tashin hankalin da yake ciki , Kamar a sama ya fara jin amon Murya ta daga nesa , tana ƙiran sa Da gudu ya nufi inda yake jin tashin sautin ta , A gefen hanya zaune cikin dusar ƙanƙara ya hango ta , Hannuwan sa duk biyu ya sa ya ɗago ta , ya riƙo kumatun ta dama da hagu , "Fatima meyasa kika fito ? Ina za ki je ?  Fatima kar ki sake tafiya ki bar mu . Ta kifta idanun ta da suka bushe ƙemas saboda sanyi tace , "Baban Mama ku na fito nema , dan Allah kayi haƙuri kar ka sake tafiya ka bar ni , bazan sake yi ma laifi ba , Kamota yayi suka miƙe tsaye , yadda take rawar sanyi ya tashi hankalin sa , " Juyawa yayi yayi durƙuso "Fatima kama ni hau bissa bayana mu je gida , Duk da wahalar da take ciki , noƙewa tayi , muryar ta na rawar sanyi tace , "Baban Mama zan iya tafiya da kaina mu taf.... Bata ƙarasa zancen ba ta ji ya ɗaga ta ciɗak , ya ɗauketa , da sauri ta riƙo rigar sa , ya nufi gida da ita . Duk da tafiyar akwai tazara amma bai gajiya ba ko dan kasancewar sa ingarman sadaukin soja ne ? Yana ajiyeta akan kujerar falon su ya shiga haɗa wuta , Muryar ta can ƙasa tace masa , "ina Mama , " zan ɗauko ta tana gidan daura da mu ,     yace Da sauri ya dawo ya zauna a gefenta ya shiga zare mata safar ƙafafunta da suka ɗau sanyi , ya zarce da cire mata hular sanyin kan ta , ɗaki ya shiga ya ɗauko ƙaton bargo ya rufa mata har kan ta Ya kamo ta ya dawo da ita gaban wutar sosai , Hannuwan sa biyu ya shiga karawa a gaban wutar su ɗau zafi sosai sai ya cire ya sa mata a ƙafafunta , A karo na biyu ta sake cewa , "Baban Mama , Mama tana waje ko ? Kar sanyi ya tada hargitsin ciwon ta , Da ido yake bin kyakkyawar fuskar ta da kallo , yadda fuskar ta ke da kyau haka ma zuciyar ta , ya aina hakan cikin ran sa , duk laifin da yayi mata , duk wahalar da ta sha a sanadin sa , ita ta lafiyar 'yar sa take , "bari na ɗauko ta , ya miƙe Har ya kai bakin ƙofa , ya waigo "Fatima kadda ki matsa dagga gaban wuta , Bai jira amsar ta ba ya fita da sauri , ya shiga ya ɗauko Mama wacce har tayi bacci , Godiya sosai ya yiwa maƙotan sa da suke musulman larabawa , Kai tsaye ya wuce da Mama Kan shinfiɗar ta ya ƙwantar da ita a ɗaki tare da haɗa wuta a cikin ɗakin , Inda ya barta nan ya dawo ya tadda ta kamar yadda ya umarceta bata motsa ba , kamar yadda bata daina rawar sanyi ba "Zanyi Sallah tace da shi , Bayan ta idar da magarib ya ja su isha'i , Da suka idar kai tsaye ya nufi shayi me zafi ya haɗo mata , Da chokali ya ɗan sisita shi ya shiga bata a baki tana kurɓa kadan-kaɗan , yadda take rawar sanyi yana damun sa dan haka ya ajiye kofin hannun sa , ya kusanto da ita sosai cikin jikin sa , bayan ya rage kayan jikin sa ya rage 'yar rigar sa ta ciki ya ware bargon da lulluɓa da shi ya rufa musu su biyu , Hannun sa ta ji ya buɗe zif ɗin rigar sanyin jikin ta , kafin ta ankara ya zura hannuwan sa ya kewaye ta da su tare da ƙwanto da ita kan kirijn sa sosai , Ɗumin jikin sa tare da firgici suka yi tasirin da suka hanata ƙwaƙwararan motsi har zuwa lokacin da ya ƙarasa zare rigar sanyin jikinta da ta ɗau sanyi na ban mamaki yayi cilli da ita gefe , Habar sa a tsakiyar kanta ya rungume ta tsam a jikin sa tana iya jin bugun zuciyar sa da yake tashi sannu kan hankali , Wani irin yanayi mai cike da daɗi da nutsuwar zuci da gangar jiki suka tsinci kan su , " Fatima , Ya ƙira sunan ta muryar sa ƙasa-ƙasa , "na'am Ta amsa masa a hankali , "Kar ki sake tafiya wani waje ke kaɗai ba tare da iznina ba kin ji ko ? Bata amsa ba illa kan ta da ta gyaɗa a hankali , Shafar bayanta yayi da hannuwan sa masu ɗumi , "Fatima ɗazu kin tsorata ni na shiga tashin hankali , kada ki ɓata a ƙasa irin US , " kayi haƙuri Baban Mama neman ku na fita sai kuma na kasa gane gida , " kan ta ya ɗago daga kirjin sa ya riƙe fuskarta ba domin yana ganin ta ba saboda duhun da yake cikin bargon , A hankali ya sumbaci goshin ta , "Na haƙura Fatima, ke ma kiyi haƙuri da faɗan da nayi miki ɗazu , kin haƙura ? " kan ta ta mayar cikin jikin sa ta sa hannuwanta biyu ta zagaye bayan sa cikin shauƙi tace "ni baka min laifin kome ba Baban Mama idan ma kayi min na yafe ma , Murmushi yayi da sauti , ya sumbaci kafaɗar ta , yana jin tilin ƙaunar ta da yake binne cikin ramsa suna tunɓuƙowa da wani irin shauƙi da yasa ya gagara mallakar kan sa a karon farko ya shiga gwada mata zallar ƙaunar ta da yayi raino tun wasu shekaru a baya da tsiron sonta ya fara ɗarsuwa a ran sa , ita ma bata ƙi ba , bata kuma bijire masa ba ta ɓuɗe tafukanta ta tallafi muradin sa , tare da miƙa masa abunda yake halalin sa .. daga falo ai sai aza room ko kuwa ??  Assalamu Alaikum Masoya ! Da fatan kuna cikin ƙoshin lafiya tare da ƙwanciyar hankali ? Ina mai baku haƙuri bisa ga jinkirin da ake samu wajen cigaba da rubutu , ajizanci ne irin na ɗan Adam. Nagode . [11/13, 7:04 PM] +234 706 503 6187: MAFARI.. ( Hargitsin Rayuwa ) Umm'muaz 38 Washegari sun tashi cikin farin ciki tare da walwala marar misaltuwa , musamman Biyamuradi Youssouf da yake jin kan sa tamkar yau ya fara angwancewa a tarihin rayuwar sa , Zallar ƙauna tare da tattali yake gwada mata da ita kuma take ta zille-zillewa tare da jin tarin nawin sa , gefe guda na zuciyar ta tsiron ƙaunar sa ya fara yaɓanya yana baza rassa . Da dukkanin daƙiƙa guda yana wucewa ne tare da tunanin sa dake manne cikin ƙwaƙwalwar ta duk kuwa da ga shi zaune zahiri a gaban ta . Yau ne Alƙawarin su da likita dan haka bayan sun kammala karin-kumallo , suka shirya cikin jibga-jibgan rigunan sanyin su rufaffu tundaga wuya, crew neck sweatshirt. Biyamuradi ya maƙalo hannuwan Falmata tare da ɗaukar Mama bisa kafaɗar sa , Ƴar tafiyar da bata cika yawa ba , mai cike da nishaɗi saboda 'yar hirar da ta gifta tsakanin su da ta ƙara musu shauƙin jin daɗin kasancewa da juna , Suka iso asibitin , babu ɓata lokaci suka haɗu da likita , bayan tambayoyin da yayi mata game da sabon cigaban da take samu kan  lafiyar ta , Cikin amsoshin da ta bashi da bincike-binciken da ya sake yi , ƙarshe ya shaida musu da cewa dole a kai ga matakin ƙarshe na yin aiki ga idon . Ba tare da ja ba Biyamuradi Youssouf ya amince , cikin lokaci kaɗan aka shigar da bayanai tare da ɗaura ta akan wasu magunguna daban da zata sha na tsawon sati biyu da za'a mata aikin idon . Sun baro asibitin zuwa gida , akan hanya Biyamuradi Youssouf ya cigaba da ƙarfafawa Falmata tare da kwaɗaitar da ita samun lafiyar idon ko da kuwa ace bata warke baki ɗaya ba . Maƙotan su suka tadda daga ƙofar su suna ƙoƙarin kulle na su gidan , Cikin mutunci Biyamuradi Youssouf ya matsa kusa suka yi musabaha da Maigidan duba da irin mutuncin da suka yi masa a jiya na riƙe masa Mama  , Balaraben da matar sa suka sake jajanta masa kan ɓacewar Falmata a jiya , Cikin jin daɗi ya sake matso da Falmata jikin sa , yana shaida musu cewa ita ce wannan , Nan ya gabatar musu da kan sa , Matar sa da 'yar sa , ƙasar da ya fito da dalilin zuwan sa nan . Inda shi ma Balaraben ya gabatar masa da kan sa , sunan sa Musa Adnan , matar sa kuma Ramlat , sai Yaran su mata biyu Hind da Zahira , Aiki ne ya kawo su nan ,  musulmai ne 'yan asalin ƙasar Kuwait . Da murna tare da ƙauna irin ta musulunci Ramlat ta matsa ga Falmata ta kama hannun ta tare da juya harshe cikin faransanci ta gaishe ta tana tambayar ƙarin lafiyar jikin ta ? , Da jin daɗi Falmata ta amsa mata ,tana riƙe hannun Ramlat da ke cikin nata , Babu ɓata lokaci Musa Adnan yayi musu tayin ko zasu bi su strong museum? Inda zasu tafi da 'ya'yan su domin shaƙatawa ? Ɗan Jim Youssouf yayi , cikin son yin nazari ,shi fa bai cika son tsawaita mu'amala da mutanen da bai wani san su sosai ba sai dai Musa ya katse masa hanzari ta hanyar bugun kafaɗar sa kaɗan , ya juya masa harshe cikin faransanci , "Allez, c'est l'un des meilleurs endroits pour emmener des enfants et des familles dans la région de Rochester am sure you'll enjoy the place. ( ka zo mu tafi , yana daga cikin jerin wurare mafiya kyau domin iyali da yara a garin Rochester na tabbatar zaka ji daɗin wajen )  Falmata wacce daman zaman waje ɗaya tsawon satika ya fara gundurar ta , ta ɗan kwanto da kan ta bisa kafaɗar sa , "BaBan Mama s'il vous plaît nous devons y aller, ( mu tafi mana ?  ) ta furta hakan tana yin ciki da muryar ta ,, Ganin sa ya kai kan zagayayyar fuskarta da take ƙyallin da ke bayyana shaidar yanayin wajen ya amshi fatar ta , Ya mayar da ganin sa ga Musa dake jiran amincewar sa ,    "Okay let's go. Cikin motar da Musa ke jaa da kansa suka kama hanya , akan hanya hira ta sarƙe a tsakanin su , inda Musa yake sanar da Youssouf aikin sa na cruise-ship worker da yake yi ƙarƙashin company jiragen ruwa na ƙasar amurka , ya cigaba da sanar da shi irin tarin ƙasashe da garuruwa gami da tsibiran da ya ziyarta wanda aikin sa ne ya bashi damar haka . Falmata da Ramlat ma suna ƴar hirar da bata cika tsawo ba saboda rashin nunan yaren faransancin a bakunan su duk biyun , yayin da ita kuma Falmata bata jin Turanci bata jin larabci yaruka biyu da Ramlat ta fi iyawa . Basu yi tafiya mai nisa ba suka iso bakin katafaren Museum ɗin , Musa shi ya yanka musu tikitin shiga ciki . Da sanya kafar su wajen ya ɗau hankalin Youssouf da yau ya taɓa zuwa , ƙwarai tsarin gine-ginen wajen suke da ban sha'awa , Mama kuwa tsalle ta fara yi ganin manya-manyan liluna da kayan wasanni irin na yara masu ɗaukar hankalin yaro har ma da babba . Da gudu ta saki hannun Falmata ta bi bayan su Hind da suka riga suka yi gaban kan su zuwa wajen kayan wasanni , Falmata tana ƙoƙarin riƙo ta , ta zille mata ,  hankalinta tashe ta shiga ƙiran sunan ta bata so ta gusa daga kusa da ita kar ta ɓata , Youssouf ya kamo hannuwanta , yana fuskantar ta , yace mata 'ki rabu da itta Fatima , kayan wassan yara ne dayawa a wajen su ta gani ta tafi wurin tare suke da sauran yara, "kar ta ɓata ko kuma ta ji ciwo Baban Mama da dai... "shitt yace yana ɗora mata yatsa akan bakin ta , "baza ta ɓata ba , zo mu tafii inda take , Yana riƙe da hannun ta suka nufi ciki , inda da ƙyar suka lalubo yaran da suka nutse cikin kayan wasanni , Mama sai ihu take me yasa aka zaƙulo ta daga cikin shirgin da ta shige ? Musa shi yayi musu jagora zuwa shashi daban-daban na kayan tarihin wasannin yara tun na tala-taini , tare da tsoffin cartoons, Suna tafe har suka ɓullo gaban gidan sasemet street  , Ɗan murmushi Youssouf yayi yana ɗage girar sa , kafin su haɗa baki shi da Mama wajen cewa, "Sasemet street ? Dariya Musa da Ramlat suke yi ganin yadda Mama take tsallen Murna , tare da ihun ƙiran sunan toys ɗin da take gani na sasemate street a waya ko Laptop ɗin baban ta da koyaushe shine cartoon ɗin kallon ta , Wanda shima kuma favorite children's show ɗin sa ne tun yana yaro hakan ya sa ya koyawa Mama ma kallon sasemate street. "Elmo , Grover, Abby, cadabby , cookie-monster,  Big bird .. Ta ƙarasa jera ƙiran sunayen su tana rufe bakin ta da hannuwan ta biyu , da gudu ta taka zuwa wajen ƴar ƙofar gidan Elmo , Tana matsa ƙararrawar ding dong ditch , ga zaton ta Elmo zai leƙo ya buɗe mata ƙofa , Kara ƙunne tayi a jikin ƙofa cikin 'yar muryar ta take ƙiran " Elmo , Elmo ouvre la porte ( Elmo open the door ) Dariyar da wajen ya ɗauka tare da hasken camerorin da suke ɗaukar ta hoto shi ya ankarar da Youssouf yawan mutanen da suka tsaya kallon shirmen da Mama ke yi cikin Burgewa , Dariya yayi ya taka wajen ta yana ƙiran sunan ta , Ɗaukar ta yayi , "Mama Elmo il dort maintenant ne le dérange pas okay ?) , elmo yana bacci kar ki tayar da shi kin ji ko ? Gyaɗa kai tayi tana waiwayen ƙofar , daga step ɗin suka tsaya Musa ya ɗauke su hoto a camerar sa , Youssouf ya kamo Falmata suka tsaya a wajen Musa ya sake yi musu wasu hotuna , Haka suka cigaba da yawatawa a strong museum , tsawon lokaci kafin su yada zango a wajen wasan pinball , nan wasan ya koma na manya tsakanin Youssouf da Musa , an tuno ƙuruciya , cike da nishaɗi da dariya suka dunga buga wasan pinball , kafin daga bisani su koma kan wasan retro arcada . Sosai suka nishanɗantu , basu yi aune ba har lokaci yayi ta tafiya, wajen cin abinci suka yada zango, Kowa ya nemi a kawo masa abunda zai ci , sanin da Youssouf yayi har yau ba kome Falmata da Mama suke iya ci ba dan haka yayi musu order na abunda zasu iya ci . Daga can wani babban fili da yake a tsaftace suka samu waje gefe , Musa ya jagorance su suka yi sallah . Hira suka cigaba da yi nan zaune bisa kan dakalin da aka yi su da kayan wasan yara yayin da yaran suka tashi suna cigaba da wasannin su da hawa kan liluna , Cikin hirar su Musa ke basu labarin wani tsibiri daya da ya taɓa zuwa a yankin Africa , cikin ƙasar Tanzania , mai suna BAWE a yankin ZANZIBAR, "Bawe zanzibar yana ɗaya daga cikin tsibirai masu kyaun yanayi da namun ruwa masu ban sha'awa tare da tsirrai masu kyaun gani da taɓa zuciya da na taɓa gani  ,      Cewar Musa , ya cigaba da cewa ya yawata a ƙasar Tanzania sosai , ya ga manyan namu dawa a cikin dazuzzukan su , wanda duk duniya a yankin ƙasashen Africa kaɗai ake samun irin su , Ya ɗora da yi masu bayani kan tsibirin Bawe da ya ƙira da dausayin duniya , Har wasu daga cikin hotunan wajen ya nunawa Youssouf daga camerar sa, Karɓa youssouf yayi yana kallon wuraren da suka yi matuƙar tafiya da hankalinsa , ashe muna da irin waɗannan dausayin masu ban sha'awa a yankin Africa ? Miƙa masa camerar sa yayi bayan ya gama ganin hotunan , ya ɗora ganin sa ga Falmata wacce ba ganin hotunan ta yi ba illa labaran da ta tsinci wasu abubuwan da Musa yake faɗa , Amma fuskar ta yalwace take da Kyakkyawan murmushin da ya ƙara mata kyau da haiba , "hannun ta ya riƙe yana murza yatsun ta , Yace, " Fatima watarana zamu raya daren mu a Bawe Zanzibar island , kina so ? Murmushi mai bayyana haƙora tayi , a hankali ta gyaɗa kai   " ina so Baban Mama , Shafar kumatun ta yayi ,yana jin yadda ƙaunar ta ke sake mamayar sa , cikin tunanin sa yana hasko yadda zasu yi rayuwa a tsibirin Bawe gefen taku . Bayan sati biyu Cikin sati biyun da suka biyo baya Falmata ta cigaba da shan magungunan da aka ɗora ta akai cikin bin ka'idar shan maganin , Gefe guda sassanyar ƙauna na gudana sannu kan hankali a tsakanin su mai cike da girmamawa daga ɓangaren Falmata , tausayi da zallar nuna kulawa kuma daga Youssouf , Duk wani rashin sakewa da ɗari-ɗarin da take da shi ta rage , ta fara sakewa da shi , har ma tana iya bashi wasu daga cikin labaran da suka shafe ta ,  iyayen ta, 'yan uwanta da garin su , Jin ainahin haƙiƙanin labarin su ya ƙarawa Youssouf zallar tausayin ta , tare da tasowar mikin binnennan laifin sa ga Yakaka , Ya haƙiƙancewa kan sa a yanzu Falmata bata da wanda ya fi shi , dan haka ya ɗau alƙawarin kome runtsi zai bata kariya cikin kowanne hali iyakar ƙarfin sa , shi zai zama inuwar hutawar ta bayan gwagwarmayar Rayuwar da suka shiga . Yau tun da suka tashi sallar asuba basu koma ba , zama suka yi yin addu'a sosai game da aikin da za'a yiwa Falmatan a yau da misalin ƙarfe tara na safe  , suna fatan Allah ya sa ayi aikin a sa'a . Sai da gari yayi haske misalin bakwai , Mama ta farka ta fara neman abin karyawa , Kamar koyaushe Youssouf shi ya yi musu abun kari da shi da Falmatan sama-sama suka ci saboda rashin nutsuwa tare da Fargaban da suke ciki . Takwas da rabi na safe ya yi musu a ofishin likita , Bayan gaisuwar da suka yi , likitan ya ƙara musu da kalmomin karfafawa ganin kamar suna tare da damuwa , A ƙarshe ya yi musu umarnin da su taso ya musu jagora zuwa ɗakin yin aikin inda sauran likitoci suke jiran su , Har bakin ƙofar dakin yin aikin da take iyakar sa ya raka ta , "kiyi ta addu'a Fatima , nima zan yi ta yi kin ji kou ? Ki roki Allah ya sa ayi aiki bissa sa'a , ki samu lafiya , Kai ta gyaɗa ,   Ba tare da ta furta kalma ba , Fuskar ta ya riƙo cikin tafukan sa  ya Sumbaci goshinta , " ki shiga Fatima da Ambaton Allah ,  Allah shi baki lafiya , "Amin    Ta amsa idanun ta na kawo ruwa , haka kawai take jin fargaba gani take tamkar zata iya rasa ran ta a garin neman lafiyar ido , Ɗaya daga cikin nurses ɗin da suke cikin ɗakin ta taho ta kama hannun Falmata zuwa ciki , Labulen da yake tsakanin su aka yaye , ya zama Youssouf yana iya hango Falmata ta tsakanin gilashin da yayi ƙawayan ga ɗakin da take ciki , A shirye ya hangota tsaf, da taimakon nurses ta kwanta akan gadon da yake tsakiyar wasu fitilu masu matsanancin haske , Ba ɓata lokaci Manyan likitocin suka matso gaban gadon suka yi ƙawayan yayin da wasu suka shiga jona mata wasu na'urori a kai , wasun su na shirya kayan aiki , Aikin da ya ɗauke su tsawon awa guda da mintoci arba'in , da Youssouf ya ji lokacin tamkar tsawon shekara , Ɗaki na musamman aka mayar da Falmata bayan an gama yi mata aikin inda zata zauna tsawon awanni arba'in da huɗu kafin a kai ga mataki na gaba , Nan suka nemi Youssouf da ya tafi gida zata kasance cikin ƙarƙarshin kulawar su , Ya so yayi gardama saboda hankalin sa da yake tashe da son sanin halin da Falmatan ke ciki , Sai da Likitan ta ya yi masa bayani mai gamsarwa tare da kwantar masa da hankali , Ya sanar da shi allurar da aka mata zata sake ta nan da wasu mintoci , sai dai sun fi son kasancewar ta ita kaɗai , a wannan ɗakin da take zasu cigaba da bata duk wata kulawar da ta dace , Hankalin sa bai kwanta ba sai da ya yi masa jagora zuwa bakin ɗakin inda ya hango Falmata a kwance kan gado , an naɗe mata idanun nata da farin ƙyalle , da alama bacci take , Sanin da ya yi Mama bata cika lafiya ba ya sa dole ya bar asibitin tare da ita ya nufi gida da zummar dawowa zuwa anjima domin ba zai iya yin har tsawon wasu awanni masu yawa ba tare da ya gan ta ba , ya san halin da take ciki ba , Ko da suka dawo gida daga shi har Mama gidan bai musu daɗi ba , Mama kaɗai ya soyawa ƙwai tare da kifin gwangwani , ita ma bata wani ci na kirki ba ta ɗauke kai , Alamun ta ƙoshi , "Mama ki ci abinci sossai mana , Girgiza kai tayi tana ƙwalan-ƙwalan da ido , "Papa mu tafi wajen Mama yanzu , "zamu tafi idan kin ida cin abincin ki kin ji kou ? Shiru tayi tana kallon sa ba tare da ta buɗe baki ta karɓi abincin da yake miƙa mata ba , Gajiya yayi da riƙe chokalin , ya ajiye gami da miƙewa yana jin yadda zuciyar sa ke cike da kewar ta , baki ɗayan hankalin sa na kan ta , Ya daɗe a zaune yana mata addu'a akan sallayar da ya idar da Sallar Azahar , Shafa kan Mama yayi wacce tayi bacci a gefen shinfiɗar sallar sa , Cikin ran sa yana aiyana irin yawan kewar Mamar ta da tayi wanda ya duƙusar da walwalarta Ɗaukar ta yayi ya kaita ɗaki ya kwantar tare da rufe ta da bargo , ya zauna daga bakin gadon , Wayar sa ya ɗauka ya latsa ƙiran layin  Tafeeda da ya yi ƙiran sa a ɗazu lokacin da ake yiwa Falmata aiki , bai samu damar ɗaukar kiran nasa ba Bayan sun gaisa , tare da Tambayar lafiyar juna Youssouf ya ɗora da tambayar sa Leila matar sa da ɗan su Imran , ? " duk lafiya suke ɗan'ouwa , Yarima kana ji na kou ? "ina jin ka da kyau ɗan'ouwa , " Yarima kou kana da labarin mutanen da ka baro shekarun baya a Nigeria ? Da ace Tafeeda na gaban shi a lokacin da zai iya hango firgicin dake zane ɓaro-ɓaro bisa fuskar sa , "waɗanne mutane Tafeeda ke magana kan su ? Tambayar da zuciyar sa ke yi ya bayyana kan harshen sa , Jim! Tafeeda ya yi yana nazartar firgicin da yake iya jiyowa daga Muryar Youssouf ɗin , "wannan ɗiya da tsautsayi yassa ta samu a duniya , nace kou ka sake waiwayar ta ? Tafiya ta kama ni zouwa Nigeria shine nake biɗar izni kan na tai na gan ta ko da ba kai tsaye ba ne na.... Cikin sauri Youssouf ya katse sa muryar sa a ɗan sama kaɗan , "Tafeeda ban ma izni ba , batun wannan ɗiya ai mun jima da ajje shi ghefe kou , ka kyale kawai wani lokaci idan Allah ya ida nufi ni naje da kaina na duba ta ,   Ajiyar zuci Tafeeda yayi , "tou babu kome 'dan ouwa Allah shi gwada mouna lokacin da lafiya , Allah kouma shi ƙara rufa asiri , 'Amin Amin 'dan ouwa , Shiru ya gifta tsakani sakamakon tunani mai zurfi da kowannen su ya faɗa , Babu shakka Tafeeda yana da wani dalili da ya sanya shi bijiro masa da zance Mama a dai-dai wannan lokacin da tsawon shekaru wajen shidda bai taɓa tambayar sa game da lamarin ta ba sai fa yau . a daddafe ya iya kaiwa bayan la'asar a gida , ya sake shirya Mama da ita ma duk ta damu da son su koma wajen Falmata , Ko da ya isa asibitin har lau bai samu damar shiga ɗakin da Falmatan take ba . Haƙuri likitar da take da Alhakin kula da ita ta bashi , akan ba zai yiwu ya shiga inda take a yau ba sai ko zuwa gobe da yammaci Haka suka ƙaraci zama daga gefen ɗakin da take ciki har duhu ya fara shiga, dan dolen sa ya miƙe da Mama ya ƙarasa jikin ƙofar ɗakin da take , Ya yi mata addu'a , kafin su bar asibitin zuwa gida , Daren ranar bai zo masa da sauƙi ba , baki ɗaya sai juye-juye yake yi ya gaza yin baccin kirki , bai san da haka ƙaunar ta ta rarake masa zuciya ba sai da ya gaza bacci saboda damuwa da son sanin halin da take ci gami da kewar ta mai tarin yawa , Abunda bai taɓa jin kwatankwacin sa kan kowacce ɗiya mace ba , ko da kuwa Maimounatu , Salon ƙaunar da yake yiwa Fatima daban ne da yake tafe da wani irin yanayi mai tasiri sossai a gare shi , Sai gefen asuba bacci ya ɗauke shi cike da mafarkai iri-iri , da har ya sanya shi makara wajen yin sallar asubahi . Tara na safe suka samu isa asibitin , inda kuma cikin sa'a ya samu damar shiga ɗakin da Falmatan take ƙarƙashin jagorancin likitan ta , Da takun ƙafar su ta san da shigowar su ɗakin da take da ita ma ta kwana cikin kewar su duk kuwa da zogi da idon ke yi mata lokaci zuwa lokaci , amma ta fi damuwa da ta san a wanne hali Mama da Baban ta suke ? "Mama , Maama Suka haɗa baki wajen ƙiran sunan junan su ita da Mama wacce da shigowar ta ɗakin ta hango Falmata , ta tafi da gudun ta , Ɗago ta Falmata tayi ta rungume ta a jikin ta , tana jin yadda sanyin ƙaunar ta ke ratsa zuciyar ta , babu shakka ƙaunar Mama magani ce ga ta ta zuciyar ,  Da murmushin samun nutsuwa ya ƙaraso bakin gadon , "Fatima yaya jikin naki ? Babu inda ke miki ciwo kou ? Baki cikin damuwa kouma ? Waigawa tayi sashin da take jin tashin muryar sa , "Baban Mama ina kwana ? Yaya Mama ta kwana ? Bata yi ciwo ba ko ?  Ɗan tsayirtawa tayi , kafin ta ɗora da cewa "bana jin damuwa ko ciwo mai tsanani , amma ina son a warware min idon nawa wannan abunda suka rufe min ido da shi yana damuna , "likitan da duk yana jin abunda take faɗi tare da taimakon na'urar kunnen sa , Ya matsa yana sake rarrashin ta tare da yiwa Youssouf bayani kan cewa kafin su warware mata idon zuwa gobe anfi buƙatar idon ya zauna a rufe haka , har sai bayan awanni arba'in , A cikin ɗakin suka wuni tare ,  sau biyu Gimbiya maimounatu na ƙiran wayar sa , ya gaza ɗaukar ƙiran .  Bai san dalili ba amma can cikin ran sa ya gujewa yin hira da maimounatu ne saboda gudun ɓacin ran Falmata . Washegari kamar yadda suka sharɗanta , awanni arba'in da huɗu da 'yan mintoci , Misalin ƙarfe goma na safe likitocin suka yi da'ira , a kan ta , Babba daga cikin su wanda kuma shine ainahin wanda ya yi mata aikin , shi ya warware mata idon , Bayan sassauta haske tare da sauya launin hasken zuwa marar kaifi , cike da fatan nasara likitan ya umarci Falmata da ta buɗe idanun ta , Babu karsashi ta fara wara idanun da suka mata wani irin nawi , hasken da ta ji kamar ya chaki idon shi yasa ta saurin runtse idanun ta kai tafukan ta biyu ta rufe fuskar ta , Cikin sauri likitar da ke gefen ta ta sauke hannunwan nata , Rarrashi da kalaman ƙarfafawa suka shiga yi mata cikin kwantar da murya , suna umartar ta da ta buɗe idon ta zata ga duniya , Sannu kan hankali ta ware idanun da suke rawa kaɗan-kaɗan , baƙon yanayi ne ya ziyarci ƙwaƙwalwa zuwa gangar jikin ta lokacin da raunanan jijiyoyin idanun ta suka fara ɗaukar jirkitattun hotuna suna aikawa da shi zuwa cikin ƙwaƙwalwarta da sauri , Wajen ya ɗauki shiru , likitocin suna ƙure ganin su akan ta da take gwale idon cike da burin son samun ƙarin ƙarfin ganin da tare kuma da son fahimtar abubuwan da take iya ganin hotunan su duru-duru , shin wannan shine hasken duniyar ? Haka kuma suffofin mutanen yake a zahiri ? A sama ta tsinto muryoyin su lokacin da suka cigaba da yi mata magana , dusu-dusu take iya ganin kusantowar motsin wani abu kafin ta tsinkayi muryar likitan yana tambayar ta ko tana iya ganin alamun motsin sa ?? Bata amsa ba illa kan ta da ta gyaɗa , Hannu ya kai yana ɗaukar wani baƙin tabarau mai haɗe da 'yar na'ura na musamman wanda cikin awanni arba'in aka yi shi domin Falmata , Ya sanya mata a fuska tare da daidaita mata shi , ya miƙe tsaye da murmushi a fuskar sa cike da burin nasara , ya tambaye ta ko tana iya ganin sa ? Zuba masa ido tayi tana iya ganin shatin sa fiye da ɗazu , suffar sa ta mutum ta bayyana duk da ba tarwai take iya gani sa ba , a hankali ta juya ƙwayar idanun ta zuwa kan kome da yake sararin wajen daki-daki take ƙure musu kallo , duk da ba sosai take ganin abubuwa ba ba kuma fahimtar su take yi ba , A hankali likitocin suka dare , tare da bada hanya ga Youssouf da Mama da babban likitan ya yi umarnin su shigo , Hannun sa yana riƙe da Mama suka shigo , Kamar koyaushe takun Mama ya fara isa ga dodon kunnen ta , Dan haka take ware ido cike da buri , burin da ada ta ɗauka ta haƙura da shi , 'yar ƙaramar halittar da ke kusantota ta ɗorawa ido , Ko ba'a faɗa mata ba , ko da cewa bata taɓa ganin wata halitta da idanun ta ba , ta san wannan ita ce Mama , " Mama , Mama ta ƙira sunan ta dai-dai da ƙarasowar ta gaban ta , Hannuwanta biyu ta sanya ta ɗago Mama , da wani irin yanayi ta matso da fuskar Mama daf da tata bayan ta ɗaura ta a cinyar ta , Ƙure mata kallo take yi , cike da son ganin ta fiye da yadda take iya hango ta dusu-dusu a yanzu , Runtse ido tayi ta buɗe a hankali 'Mama    Ta ƙira sunan ta,  Dariya Mama tayi tana ɗora 'yan hannuwanta akan hannun Falmata da take tallafe da kumatun ta , Ta ga hasken haƙoran Mama da fuskar ta , a yanzu ta yadda da cewa ta samu waraka , irin ganin da take yi dusu-dusu shine ganin da ta haƙiƙance kowanne ɗan adam yana yi , Irin haske marar ƙarfin da take gani shi ta aminta da cewa shine hasken duniya , ita kuwa mai zata yi da ya wuce godiya ga Allah da ya nufe ta da samun waraka ? rungume Mama tayi tana faɗin kalmar Alhamdulillah , Alhamdulillah babu ƙaƙƙautawa , Raf-Raf-Raf likitocin da suke wajen suka ɗau tafi , cike da bayyana farin cikin su na samun nasara kan aiki , Youssouf wanda farin cikin sa bazai misaltu ba ya tako zuwa gaban gadon Falmata , " Fatima Ya ƙira sunan ta , da amon muryar da take cike da shauƙi da zumuɗi , cike da ƙwaɗayin son ganin Fuskar wannan ma'abocin Alheri a gare ta ta ɗago kan ta daga fuskar Mama da take ta son sake gani tamkar mai son haddace kamannin ta a ɗan tsakanin lokacin , Dariyar haƙoran sa ta fara cin karo da su , kafin hasken farar fuskar sa irin na Mama da ta fahimci basu kai sauran mutanen wajen haske ba , ta bayyana mata ,  Kafe shi tayi da ido tana burin ganin kamannin sa ko da kuwa ace shine abu na ƙarshe da zata iya samun nasarar gani kafin hasken da ta samu ya koma duhu da har yanzu ta gaza yadda a zahiri ne ba mafarki ba cewa idanun ta suna ganin duniyar da ta rayu tsawon lokaci a cikin ta , Irin riƙon da ta yiwa fuskar Mama shi ta masa , ta kai hannun ta kan sajen fuskar sa ta tallafo fuskar tana kallon sa da irin ganin da ya sawwaƙa a gare ta  , Dariya Youssouf ɗin ya cigaba da yi da haƙoran sa ganin yadda ta riƙe masa fuska ƙam-ƙam , kamar wanda zai ƙwace ya gudu , ko kuwa ya ɓace mata , Da ƴar dariyar mai tafe da amon da  ke bayyana tsantsar farin-cikin ta , ta kai goshin ta ta haɗa da nashi , tsinin hancin su na gugar na juna , "Baban Mama nagode , nagode nago...   "Fatima ki godewa Allah da ya baki lafiya , ni ma shi nake godewa , da ya nufa aka cimma nasarar aiki , Zama yayi daga gefen ta a bakin gadon , Mama tana tsakiyar su ya sanya hannu sa ya kewaye su da shi ya rungumo su jikin sa , yana jin matsanancin farin-ciki na zagaya ruhin sa , Tamkar a ire-iren shuɗaɗɗun lokutan da suka wuce cikin rayuwar ta da Yakaka , sautin ta ya bijiro cikin tunanin ta tamkar a lokacin take furta mata , " Falmata na ina ji a jikina watarana za ki warke , za ki ganni kamar yadda nake ganin ki . Hawaye masu ɗumi suka silmiyo ta ƙarƙashin gilashin idanun ta , kewa tare da ƙaunar ahalin ta suka bijiro mata , a sarari ta furta " Allah ya jiƙan ku Baba , Mama , Yakaka,  Bakura da Baana , 'Amin  Youssouf ya amsa mata . ***** Cike da tarin sabbin dokoki da sharaɗin ziyartar likita a duk bayan mako guda na tsawon watanni biyu , Suka samu sallama daga asibitin , tafiyar ƙafa suka yi zuwa gidan su , inda Falmata ta dunga bin titi da ganin ta marar ƙarfi , Murna fal cike da zuciyoyin su ita da Youssouf , kome ta hango shatin sa sai ta tambaye shi wannan abun menene shi ? Meye sunan sa ? Shi kuma babu gajiyawa cikin jin daɗin tambayoyin da take masa yake bata amsa tare da faɗa mata sunayen abubuwan . Ƙofar gidan Musa suka tsaya , farin cikin da zukatan su ke ciki ya tunbatsa so suke su yi ɗaukanin sa da wani , alhalin babu wani nasu makusanci tare da su , dan haka gidan Musa suka yada zango , Musa da Ramlat sun taya su murna sosai inda a ƙarshe har 'yar walima suka shirya musu nan cikin falon su, Yana riƙe da hannunta suka shigo gida , Suna shiga tun kafin su zauna ta ce  shi , "Baban Mama ka ƙira Hajja a waya na faɗa mata na warke nima yanzu ina gani , Yana murmushi ya zaro wayar sa daga Aljihun sa ya shiga lalubar layin Hajja , Ya san dole tana neman wani makusanci nata wanda zata raba farin-cikin ta da shi , Nigeria Tsawon satikan da suka biyo bayan Rayuwar Yakaka tayi su ne wajen ganin ta cigaba da ƙokarin wanke laifin ta daga idanun jama'ar gidan Prof , Babu inda take zuwa kullum tana gida ita ke yin mafiya yawan aiyukan gidan , A hankali Hajja ta fara fahimtar kyawawan ɗabi'un Yakaka , na kawaici da gudun tashin hankali , sannan kuma me sakakkiyar fuska ce ma'abociyar murmushi ,uwa uba yawan ibadar da ya zauna mata . Hakan ya sa ta fara sakar mata fuska har takan ɗan ja ta da hira a wasu lokutan , A yau ma zaune suke , suna 'yar hira Yakaka tana taya Hajja tsinke ganyen zogalen da zata yiwa Prof girki da shi Wayar Hajja da take ajiye a gefe ta ɗau ƙara , Da sauri Yakaka ta ɗau wayar ta miƙa mata , "Ni hauwa'u waye ke ƙirana da wannan sanyin la'asar ɗin ? Allah jishe mu Alheri , ɗaga ƙiran tayi dai-dai da ƙwanƙwasa ƙofar falon da aka yi , Yakaka ta miƙe da saurin ta tana cewa " Oyoyo Rahima . Ta nufi ƙofar , "Assalamu Alaikum Hajja ni ce Falmata , Muryar Falmata ta karaɗe kunnen Hajja ta cikin wayar ta mai maɗaukakin sauti , Yunƙurawa tayi ta miƙe tsaye ɗingis-ɗingis ta nufi ɗakin ta da yake gefe , "Lale Lale Marhabin da uwarɗakina Fatima mutan turai , Ta furta hakan lokacin da take ƙarasa shigewa ɗaki cike da son kar Yakaka ta san da wacce take waya , " Uwarɗakina ince dai duk kuna lafiya ? Ya Babban soja tare da 'yar rigima Mama , dafatan an samu nasara wajen neman magani ? "Hajja Alhamdulillahi ki taya ni murna , na warke Hajja na samu lafiyar idona , "Da gaske Fatima kai Alhamdulillah nayi murna , nayi murna Allah Abun godiya kin warke Fatima ,? Buwayi gagara misali , Murnar Yakaka ta rikiɗe zuwa Fargaba lokacin da idanun ta suka sarƙe cikin na Sofi matar Yaya Dakta , Kallon-kallo na daƙiƙoƙi suka yiwa juna kafin ta tsinkayo muryar Doctor Hamza wanda yake tsaye daga bayan sofi ,   "Malama kauce ki bada guri mutane su wuce kin yi wani sanƙanƙam a tsaye kina zarewa mutane ido , Da sauri Yakaka tayi baya tana komawa falon ƙarƙashin rakiyar mummunan tsakin da sofi ta bita da shi . Ɗan diri-diri tayi a falon rashin ganin Hajja yasa sum-sum ta nemi mafakar ta a can ƙarƙashin kafar benen da yake falon ta samu guri ta zauna ran ta duk a dagule . "Me ya sake dawo da shi yau kuma ? har ma da matar sa ? Daga inda take tana iya jiyo tashin Muryar su , Da Sallamar da Docto Hamza ya yi , Basu ko zauna ba Sofi ta fara faɗin "Wannan kuma wacce jemammiyar 'yar aiki aka samu haka a gidan nan ? Sai tashin ƙarnin man masu bleaching take ,  Doctor ba dai ita take yin wanke-wanke ba , ? Dan bana jin zan iya riƙe ko chokalin da ta wanke , A kaikaice Doctor hamza ya dube ta yana samarwa kan sa mazauni akan kujerar falon mai cin mutum guda , Motsa laɓɓan sa yayi kamar zai ce wani abu sai kuma yayi biris da ita yana zaro wayar sa daga Aljihu , Hannun kujerar da ya zauna ,Sofi tayi matsuguni a ɗosane tana cigaba da cewa , "Ni kamar ma nasan Fuskar ta a wani waje ? A hankali ya ɗago kai yana duban ta da ita ma ta karkato gare shi , fuskar ta ɗauke da wani irin yanayi na tsantsar ɓacin rai da bai kai ga sanin dalilin samuwar sa ba , " akan wa kike magana ne ? " wannan yarinyar mai kama da farar kura , " Ta furta hakan lokacin da tunanin ta ya gama tuno mata da inda ta taɓa ganin Yakaka a gidan Samy baby , Dariya ce ta so kama Doctor Hamza jin an kwatanta Yakaka da farar kura ,      " ko ina sofin sa ta san wannan gantalalliyar yarinyar ?        Ya tambayi kansa a zuci . " okay , Yace a taƙaice yana mayar da hankalin sa ga fuskar wayar sa , "irin karuwan nan ce masu tsayawa a bakin hanya suna ne... Fitowar Hajja cikin Murna ya katse mata zance da ta ɗauko yi , " a a' ah Babban likita kaine tafe iwar haka ? Sannu da zuwa sannu da zuwa ka sha hanya tun daga birnin tarayya, Da 'yar fara'a Doctor Hamza yake amsawa Hajja gaisuwar da take masa , Hajja ta ɗora ganin ta kan Sofi wacce ta jirkita sosai kan kafaɗun Doctor Hamza kirjin ta daf da fuskar sa , fiye da rabin cinyar ta na kan jikinsa ,  kan ta a ɗage sai shan ƙamshi take , ko ƙala bata cewa Hajja ba , "ah to wacece ita 'yar aikin zata gaisar ? Ƙanƙan da ido Hajja tayi , " Yau ina ganin taɓara maigida da kukan tsarki , mene haka wata shaɓatartar da ke kin wani ɗaɗɗane ɗan mutane ƙin kalmashe shi ? O ni hauwa'u inda ranka ka sha kallo , ikon Allah 'ya'yan zamani , mu lokacin mu ina muke iya ɗaga ido mu dubi miji a gaban mutane ? Cike da 'yar kunya doctor Hamza ya miƙe bayan ya ture Sofi daga jikin sa ,  yace , " Rahima bata nan ko Hajja ? A ɗan sama mana abinda zamu ci please ina tare da yunwa , " Rahima bata nan likita , bata ƙaraso ba daga Makaranta , to babu laifi yanzu kuwa za'a samar da abinci ,sannun ku da hanya , Wani banzan Kallo Sofi ta jefawa Hajja tana bin bayan mijinta , cikin ranta cike da haushin kalaman Hajja , cikin ran ta tana cewa , "ji min tsohuwar nan da kinibibi ? Ko ina ruwanta da ni ," ? Idan har ta ce zata shiga harka ta kafin na bar gidan nan sai na ratsa mata tarbiyya ,' " Mts   Hajja ta saki tsaki bayan barin su falon , "abun haushi Nama na jan kare ,  me ake da mace marar kunya da kamun kai ? Kunya ai ado ce . Murnar labarin da Falmata ta bata na samun warakar ta ya taso yayi awon gaba da takaicin da sofi ta bata , ***** Washegari bayan Doctor Hamza ya shirya kai tsaye ya nufi yin abunda ya kawo shi garin . Bayan ya je sun gaisa da Prof shi da Sofi , daga bakin mashigar sashin Prof ya dakatar da ita daga binsa , " Sofi ki koma ciki , ni fita zan yi sai na   dawo , Zunɓur-ɓur ta turo baki ,    Cikin salon da koyaushe take amfani dashi idan tana gaban shi na ƙoƙarin ta nuna masa ƙuruciyar ta da a zahiri ta riga ta yi mata adabo ,         A shagwaɓe tace "Haba mana Doctor please zan bika mu tafi tare naga gari , ka ga fa irin yanayin gidan shiru ba... "please Sofi kar ki ɓata min lokaci a banza ai kin san yanayin gidan babu abokin hira kika dage sai kin biyo ni , kuma ni wajen aiki zan tafi ba yawo a gari ba ,   Juyawa yayi ya ƙarasa ga motar sa ya shige ciki bai ko sake waigowa ta kan ta ba ya tada motar yayi tafiyar sa , " jagale ! Tayi a tsaye ranta cike da ƙuna ,     "so take ta san meye Doctor yake ƙullawa a garin da yake ta zirga-zirga a tsakanin Maiduguri da Abuja , Cikin wata guda wannan ne zuwan sa na uku , ita fa duk wani abu da zai sha gaban ta , ya mata katanga kome ƙanƙantar sa da Doctor Hamza yaƙi take yi da koma menene , Ko aikin sa dan bata da ikon hana shi ne amma da tuni ta shata layi tsakanin su , so take koyaushe ya zama bashi da uzuri sai nata , A fusace ta juya ciki , **** Kai tsaye gidan Amne ya nufa , ya taddata tana karin kumallo da Fankaso da miyar gandar ƙafar sa , Ya gaishe ta cike da ladabi , ta amsa tana mai farin-cikin ganin sa , Tambayar sa tayi ya safiyya ? Ya shaida mata ai tare suka zo garin . "Shine kuma baka kawo min ita mun gaisa ba ? Ta furta haka lokacin da take zuba masa miya akan fankason da ta zuba masa , "Amnee fita zamu yi tare zuwa wani waje , Ya furta haka lokacin da yake kai lomar farko bakin sa. " ina kuma zamu ? Allah yasa dai Lafiya . "lafiya lau Amne sai Alheri , cikin nutsuwa ya gama cin abincin sa , Bayan ya wanke hannu , yace "Amne zamu iya tafiya yanzu ko kina da wani uzurin da zaki yi ? "ba abunda zan yi , amma tukun wai ina zaka kai ni ? Kaƙi sanar da ni . "kiyi haƙuri Amnee mu je ki gani , "to bari na yafa mayafi na , Tare suka fito shi da ita ya buɗe mata gidan baya na mota ta shiga ya rufe , gami da zagayawa ya shiga ya tada motar yana barin unguwar , Ya riga ya gama tsara hanyoyin da zai bi domin ganin ya dai-daita lamarin iyayensa , wanda daman burin sa ne tun ma kafin bayyanuwar Khaalty Rahima a gare shi , Bayyanar ta ya sauƙaƙa masa lamarin , ya kuma ji daɗi domin yasan dawowar ta a dai-dai lokacin matakin nasarar gyaruwar kome ne wanda hargitsewar kome yake da nasaba da ita , Bayan duk lallamin da yayi mata akan  ya mayar da ita gida , amma taƙi amincewa , Cikin dogon nazarin da yayi ya yanke shawarar haɗa su kitsumun , ba tare da sanin kowaccen su ba . Dan haka a yanzu da ya ɗau Amnee kai tsaye ya nufi gidan da Khalty Rahima take ba tare da ya sanar da kowaccen su game da 'yar uwarta ba . Suna 'yar hira shi da Amnee har suka iso ƙofar gidan , ya fita a motar ya nemi iznin shiga gidan daga maigadi inda ya amince nan take har ma yake sake jaddada masa , ai kuwa Mamar Bulama tana , Tare da Amnee suka shiga wacce take cike da mamakin ina Hamza ya kawo ta ? Gurin wa suka zo ? Allah dai ya sa lafiya , Shi ya fara shiga sashin da Khaalty Rahima take , daga bakin ƙofa ya dogare ,  yana fuskantar Cikin gidan daga inda yake yana hango Khaalty Rahima wacce ta duƙufa yin wanki daga gefe , Babu Alamun ta san da tsayuwar sa a wajen , "Bissmillah Amnee shigo , " Assalamu Alaikum , Amne ta ce lokacin da ta shigo filin gidan , Dai-dai da ɗagowar Khaalty Rahima wacce sautin Hamza ya ankarar da ita tsayuwar shi a wajen , Zuciyoyin su suka buga da wani irin yanayi mai girma , daga ƙasa har sama Amnee take kallon ta , Kowanne irin jirkituwar halitta ce ta samu Rahima ƙanwar ta , ba zai sa ta gaza gane ta ba , "Rahma,  Rahmatullah , Ta ƙira ta da wani ɗan guntun sauti , "Rahmatullah hal hdha haqiqiun lak 'Yaa ukhtee ? ( shin dagaske ke ce 'Yar uwata ? ) A hankali ta saki rigar hannun ta da take wankewa  , Da hannu biyu Amnee ta rufe fuskar ta lokacin da hawayen farin-ciki ya fara zarya akan fuskar ta , Bata jira ƙarasowar Rahima ba wacce take tahowa da sassarfa , ta taka da sauri ta tadda ta , Rungume juna suka yi hawayen murnar ganin junan su na sauƙa , Khaalty Rahima bata san haka take cikin maricin tare da kewar 'yar uwar ta , yayar ta , madadin uwa agare ta ba sai yanzu da ta gan ta tsaye a gaban ta bayan tsawon shekaru fiye da ashirin da suka kwashe basa tare . Hannu biyu Amnee ta sa ta riƙe fuskar Rahima , "ke ce wannan Rahimatullah ? Meyasa kika tafi kika barni ? Kina garin nan Rahimatullah duk tsawon shekarun nan bakya nema na ? Meye na miki mai girma haka Rahimatullah  ? "Rahimatullah wacce irin Rayuwa kike yi tunda kika barni ? Nan ne gidan ki ? Kin yi aure ne ? Ina maigidanki ? ki min magana mana ƙanwata Muryar Doctor Hamza ta ratsa tsakani , shi da kansa ƙwalla ta taru masa a ido , irin ƙaunar da yake hangowa a fuskar kowaccen su ga 'yar uwar ta , ta masa yanayi da na yaran nan biyu 'yan gudun hijira . "Amnee ki kwantar da hankalin ki , Khaalty Rahima ta gamu da larura tana jin magana amma bata iya mayarwa , Sabon Kuka Amnee ta fashe da shi , "Rahimatullah ce ta kurunce ? Meye haka ya faru da ke Rahimatullah ? Cikin ruɗani ta waiga ga Hamza " mu tafi asibiti a duba min ita yanzu Rahimatullah Amana ce a wajena , Da sigar rarrashi khaalty Rahima ta jijjiga hannun Amnee da yake cikin nata , Waigowa tayi tana kallon ta , Murmushi tayi mata , ta kai hannu ta goge mata hawaye tana girgiza mata kai , ƙoƙarin taro ta Amnee take lokacin da ta ga tana ƙoƙarin tsugunnawa , tare suka durƙusa , Khaalty Rahima ta rubuta mata a ƙasa cikin yaren su , "ki daina kuka , murna yakamata muyi da sake ganin junan mu Yaa Amina . Bayan Awanni biyu Doctor Hamza , tare da Amnee da Khaalty Rahima da Bulama suka kama hanyar komawa gidan Amnee. Ga mamakin Hamza Khaalty Rahima bata yiwa 'yar uwarta irin tirjiyar da tayi masa kan komawa gida ba , Ko daman dan bata ga 'yar uwar tata bane a gaban ta ? abunda ya ɗan riƙe su a gidan shine batun tafiya da Rahima da ɗan ta da suka yi wanda da farko matar da khaalty Rahimar take yiwa aiki bata Amince ba . sai da suka bata gamsassun bayanai tare da ƙwararan hujjoji ta kuma ga shaida tare da Amincewar ita kanta Khaalty Rahimar tukun ta yarda ta sallami Rahima tare da yi mata fatan Alheri . Da shigar su gida Amnee ta shiga hidimar Khaalty Rahima , kama daga shirya mata wajen zama na musamman har zuwa gyara mata shimfiɗar da zasu kwana ita da ɗan ta. Abunda ya sake bawa Hamza tausayi shine duk inda Amnee ta gusa , Khaalty Rahima zata matsa kusa da ita tana yunƙurin karɓe aikin da take yi , Amnee taƙi sakar mata , banda murmushi mai cike da tarin ƙauna da tausayi babu abunda suke yiwa junan su . Sai da Amnee ta gama gyara musu waje tsaf sannan ta dawo ta zauna kusa da Rahima , ta riƙo hannun ta tace , "Rahimatullah ina son jin labarin yadda kika yi rayuwa bayan barin ki gida , amma babu dama a yanzu , inshaAllah daga gobe zaki fara ganin likita , Gyaran murya Doctor Hamza yayi , "Amne Ya ƙira sunan ta , a hankali ta waigo gare shi , "Amnee ina son dan Allah yau ki bani labarin abunda ya faru da rayuwar ku ke da Baba da Khaalty Rahima ? Dan Allah kar ki ƙi , ki ban labarin a matsayin tukuicin dawo miki da Khaalty Rahima da nayi . Shiru tayi na wani ɗan lokaci , kafin ta sauƙe ajiyar zuciya , *** "Labarin ba wani mai daɗi bane da kake naciyar sanin sa , "Kamar yadda ka sani ne mu 'Yan asalin ƙasar Chad ne daga Babban birnin N'Djamena , inda aka haife mu , iyaye da dangin mu baki ɗaya.  "Mahaifin mu sajjan ne ( mai gadin gidan yari )  a babban alsijn na ƙasar mu , albashin sa bai cika yawa ba dan haka mai ƙaramin ƙarfi ne sosai , dangin sa duk talakawa ne ,  haka ma mahaifiyar mu ta fito daga gidan talakawa sosai , sana'ar iyayenta sarrafa gishiri daga bakin teku su kawo cikin gari su sayar , ni ce Babbar  'yar su sai ƙanne na maza huɗu "Salihu , Mohammed , Usman da Jamil  sai ƙaramar mu Rahimatullah . "Rahimatullah tana shekaru biyar ni ina da goma sha shida Mahaifiyar mu ta rasu , inda ba'a ɗau lokaci ba bayan mutuwar ta Maifinmu ya sake yin aure , ya auri wata mata mai 'ya'ya huɗu daga ƙabilar N'gambaye mabiyar Adinnin Christian ƴar ainahin ɗarikar Roman Catholic . "zuwan "Aichawa rayuwar mu shi yayi sanadiyyar faɗawar mu ƙunci domin Aicha irin mugayen matan nan ce marar imani , babu irin aikin wahalarwa da bata sanya mu , Su salihu sun zame mata masu nemo mata kuɗi , inda ni kuma na zama baiwar ta mai yin duk wasu aikin cikin gida, hatta Rahimtullah da take ƙanƙanuwa bata tsallakewa izaya daga hannun Aicha ba . "shi da kansa Mahaifin mu bai tsira ba daga bala'in ta dan a wasu lokutan har duka take yi masa , idan ta nemi kuɗi bai bata ba, hakan ya sa yake masifar tsoron ta ba shi da kataɓus , ya auro jaraba . "mugun neman kuɗi irin na Aicha ya sa nima ta sama min aikin goge-goge a babban ofishin jakadancin ƙasar mu tun a wancen lokacin da ba'a cika barin 'ya'ya mata fita neman kuɗi ba , "karatu ma alokacin iyakata primary ban ci gaba ba .  "da murna na fara zuwa aikin saboda ganin zan huta daga masifar Aicha da wahalar aikin gida , sai dai kuma tunanin Rahimatullah da zan dunga bari a gida ya rage min karsashi , " ganin cewa aikin nawa shara ne da goge-goge sai na nemi iznin na dunga zuwa da Rahimatullah tana zama a gefe ni nayi aikina , saboda nasan idsn na bar ta a gida azaba za'a dunga gana mata , cikin sa'a aka amince min . "Tafiya ce miƙaƙƙiya a ƙafa daga unguwar mu zuwa wajen aikina , amma haka nake goyon Rahimatullah daga alfijir ya keto mu ɗau hanya , kafin lokacin da muke isa gari ya waye sosai , "Haka zan yi aikina Rahimatullah tana ƙiriniyar ta , "Rahimatullah irin yaran nan ce masu son wasa , hakan ya sa sai ina aiki ina kaffa-kaffa da ita kar ta yi musu ɓarna dan wani lokacin ma sai na neme ta na rasa ta shige ƙarƙashin tebura ko tayi wani wajen , "Amne ta tsagaita tana duban fuskar Khaalty Rahima wacce take murmushi , "Ashe Bulama ba a ƙasa ya tsinta ba gado yayi ,   Doctor Hamza ya kitsima hakan a ransa , Amnee ta cigaba da cewa , "Na ɗau tsawon watanni shida ina aikin goge-goge a ofisoshin guda biyar kafin a rage min yawan su zuwa kula da ofishi biyu rak , na wata mata Basudaniya ( Sudanese )"Mademe Laura , da kuma na wani jakadan ƙasar Nigeria "Al-Mustafa Dilmari . "tsakanina da su Gaisuwa msi cike da girmamawa ne idan sun iso ofis sun tarad dani a bakin aikina , "wata alaƙa bata taɓa gifta tsakanin mu ba sai Ranar da Rahima tayi wata mummunar ɓarna a ofishin Ambassador Mustapha , inda ta yayyaga wasu takardu masu muhimmanci da ya mance ya tafi ya bar su a ofishin sa ba tare da ya adana su ba , "Ranar na shiga tashin hankali domin kuwa faɗa sosai ya dunga yi min , bai tsagaita ba sai da Rahimatulla wacce take goye a bayana , saboda zamu tafi ƙiran sa ya cimmin , ta leƙo da kanta cikin harshen larabci ta ce da shi yayi haƙuri ya daina yi mana faɗa irin yadda Aichatuwa take yi mana kullum ai ita ta yaga takardun tana so ta yiwa ƴar tsanar ta kaya , "Ban san dalili ba sai naga ya sassauta fishin sa , a ƙarshe yace mu tafi kawai , "tun daga ranar sai naji tsoron sake zuwa da Rahima domin kar tayi wata ɓarna sa zata sa a kore ni daga aikin wanda albashin sa a lokacin da shi nake yi mana hidimar yau da kullum  ni da ita duk kuwa da cewa kaso uku Aichatuwa take raba albashin ta ɗau kashi biyu da rabi ta bani guntun , "daɓ dole nake barin ta a gida tana kuka , wani lokacin nima har ta saka ni ƙwalla , nake tafiya na bar ta , "ba'a yi sati guda ba wata safiya har na kammala aiki zan tafi , Ambassador Al-mustapha ya ƙira ni , zuciyata cike da tsoro na je na ɗauks batun laifin Rahima ne bai wuce ba ko kuma ni ce na sake yin wani laifin . " ga mamakina sai naji yana tambayata ina ƙanwa ta take meyasa na daina zuwa da ita ? " na ce masa tana nan , inajin tsoron kar ta sake ɓarna shiyasa na daina zuwa da ita , " sai ya umarceni da mu cigaba da zuwa tare amma na dunga lura da ita kar ta dunga yin ɓarna , "shikenan Tun daga ranar na cigaba da zuwa da Rahima , "a hankali sabo mai ƙarfi ya shiga tsakanin Ambassador Al-mustapha da Rahimatullah saboda 'yan kayan maƙulashe na yara da yake mata hasafin su , "kafin wasu watanni shaƙuwar su da Rahima ta shafeni wanda a ƙarshe cikin shekara guda tsakanin mu ya rikiɗe ya zama soyayya ce mai ƙarfi , "duk kuwa da tazarar matsayi da yake tsakanin mu hakanan Allah ya kulla auratayya a tsakanin mu , bayan rigin-gimu da suka taso daga dukkan ɓangarorin biyu , daga Aichatuwa , da bangaren iyaye da 'yan uwa Al-mustapha na jini , wanda suks tirje akan ba zai auri 'yar wata ƙasa ba wacce ba ƙabilar su ta kanurai ba , alhalin ga 'yar uwarsu wacce take dakon jiran sa suyi aure , "hakanan ɓangaren Aichatuwa wacce ta bi duk wata hanyar da zata iya bi domin ganin auren mu bai yiwu ba da Mahaifin ka , amma dayake shi aure Kaddara ce daga kaddarorin da Allah yake yi ga bayin sa . "A ƙarshe aka ɗaura Auren mu ni da Mahaifinka tare da Amincewar kakan ku wanda ya taka har ƙasar mu ya nemawa ɗan sa aurena cikin mutuntawa , bai duba ƙasƙancin mu da shi yake babban Attajiri a ƙasar su kuma mai ilmin addini da na boko tun a wancen zamanin . " Bayan auren mu mun zauna shekara guda a N'Djamena kafin aikin mahaifin ku ya ƙare da ƙasar mu , muka kuma fara shirin komawa ƙasar su , "a kuma tsukin wannan lokacin Allah ya yiwa Mahaifin mu Rasuwa sakamakon sukar sa da wuƙa da wasu ga cikin 'yan firsina suka yi a ƙoƙarin su na gudu daga gidan yari . "Mutuwar Baban mu ta gigita mu ganin cewa duk wani gatan da muke da shi ya ƙare , "a ƙarshe dole muka haƙura , riƙon Rahima kachokam ya dawo hannun mu da duk wasu ɗawainiyar ta Al-Mustapha ke yi , "Sauran ƙannena maza suka raɓu da gidajen 'yan uwa  , , "Ba mu jima ba bayan nan muka koma Nigeria tare da Rahimatullah da   kuma kai a lokacin kana ɗan jariri . "na fuskanci tsangwama da ƙiyayya iri-iri daga kakar ku , da dangin mahaifin ku da baki ɗayan su basa ƙaunar auren mu , idan aka ɗauke Salman wanda ƙani ne na uku ga mahaifin ku da shi babu ruwan sa da duk wasu lamura da suka shafe ni . "Haka shekaru suka yi ta tafiya tare da nasarar rayuwa , matsala mafi girma da ta zama sanadin rabuwar auren mu da mahaifin ku ya samo asaline daga lokacin da Soyayya ta shiga tsakanin Salman da Rahimatullah , "lokacin Rahima ta gama makarantar gaba da primary , kai kuma ka shiga makarantar kwana ta gaba da primary , "rikicin an ɗauki lokaci ana yin sa tun bayan bayyanuwar soyayyar su da suka yi shekaru biyu suna boyen ta a tsakanin su , "Salman ya doshi mahaifiyar su da sauran 'yan uwan sa da batun auren Rahimatullah , ƙaramin yaki aka yi a tsakanin su saboda lokacin kakan ku ya jima da rasuwa . "Lamari yayi tsamari da yasa har kakar ku ta ƙira mahaifinku ta masa kashedi kan muddin yana son Albarkar ta , ya zama dole ya raba tsakanin ƙanwar matar sa da ƙanin sa , "daga lokacin shima Mahaifinku ya fara nuna adawar sa da soyayyar tsakanin Salman da Rahima domin bin umarnin Mahaifiyar su , da hakan ya kawo saɓanin a tsakanina da shi domin ni ɗari cikin ɗari nake tare da su akan lamarin soyayyar su . "ana cikin wannan hatsaniyar uwar matar da aka so aurawa Mahaifin ku wacce take ƙanwar kakan ku ce ta zo da wani lamari mai yanayi da tsafi ko kuwa chanfi  , kan cewa muddin ba'a yi gaggawar raba tsakanin Salman da Rahima ba to babu makawa guda a tsakanin su zai mutu , domin Malamin ta yace babu aure a tsakanin su , ' "Maganar bata ɗaga min hankali ba sai da naga kamar Mahaifinku ya yarda da batun inda har ya fara maganar ko dai Rahimatullah zata koma N'Djamena na ɗan wani lokaci , idan kome ya lafa ta dawo ,ranar nayi kukan Maraicin mu da rashin gatan mu  , " an yi haka bai fi da wata guda ba , Rahima ta gama shan kukan ta akan wannan batun , Babban Al'amari ya afku, "Ranar wata juma'a bayan Rahimatullah da Salman sun gama hira da rabin ta neman hanyar warwaruwar matsalar su suke tare da kaiwa ga cikar burin su , "ƙarfe biyu da rabi na ranar bayan sallar juma'a labarin Rasuwar Salman Dilmari matashin Saurayi, ya bazu tare da yin tambari a baki ɗayan birnin Maiduguri kasancewar sa matashin ɗan siyasa da ya yi suna a lokacin , "ya rasu a sakamakon mummunan haɗarin mota da yayi akan hanyar sa ta komawa daga masallacin juma'ah mintoci arba'in da rabuwar su da Rahima , " mutuwar data girgiza zukata da dama , ta kuma bar miƙi a zuciyoyin wasu da dama , Salman Mai Alheri ne , Allah ya gafarta masa , Shiru ne ya ratsa tsakanin su saboda kuka haiƙan da Rahima take yi , kukan tasowar tsohon miƙin dake zuciyar ta da ya tarad sabon ciwukan dake cin ranta a kullum kwanan duniya , Mutuwar  mijinta uban 'ya'yan ta da ta tarar da gawar sa a yashe cikin gona , haka kuma tana ji tana gani ta tsallake shi domin ceton ranta da na 'ya'yan ta ta tafi ta bar gawar sa a daji,  tare da ɓacewar manyan 'ya'yan ta da har yau bata da sanin haƙiƙani kan rayuwar ko mutuwar su ta ma fi haƙaƙewa akan Yakaka da Falmata sun mutu kamar yadda harsashi ya samu Baana yayar Bulama ta mutu akan cinyar ta , Bakin lafayyar ta Amne ta sanya ta sharewa Rahima hawaye sannan ta cigaba da cewa , "Fasalta irin halin da baki ɗayan zuri'ar Dilmari ta samu kanta a ciki bashi yiwuwa ,   "ai ka san lokacin kana da wayo sosai kana secondary School , gyaɗa kai Hamza yayi wanda idanun sa suka yi jaa , " Rahima ta shiga ɗimuwa marar misali domin har suma ta dunga yi , sai da Maigadin gidan ku na lokacin ya dunga yi mata rubutu , cikin sati guda da mutuwar sa Rahima ta rame tamkar majiyanciya , ni da kaina ƙarfin hali nake yi , nake hana kaina tunani saboda tsohon cikin Rahima ƙarama da nake ɗauke da shi . "abu mafi muni da ya biyo bayan mutuwar Salman shine takowa da 'yan uwansa suka yi har gida bayan kwana arba'in da mutuwar sa , suka ci mutuncin mu ni da Rahima , a ƙarshe suka danganta mutuwar Salman da cewa ni da Rahima muka lashe masa kurwa muka kashe shi , to waye ya san salsalar asalin mu ?? "Ni kuka Rahima kuka , sannan abun takaicin mahaifinka yana zaune ya gagara hana su ko ɗaukar wani mataki na ba mu kariya , wanda hakan ni kuma ya tunzuro ni , na yunƙuro domin maida musu martani a karon farko bisa duk abubuwan da suke min marasa daɗi , "Ga maɗaukakin mamakina sai mahaifinka ya hayyaƙo min ya takore ni daga yin magana har ma yace muddin nace wani abu kome zai iya faruwa ga igiyoyin auren mu , "bisa tilas nayi shiru sai hawaye da muke yi ni da Rahima suka gama zage mu tas har da dungurin Rahima da alama ma duka suke da niyyar yi mata sai ɗan uwansu ya rarrashe su , 'tundaga wannan ranar Rahima ta sake yin sanyi duk ta susuce firgici ya bayyana cikin suffar ta bata da aiki sai tunani   , "duk da ceqa ina bin duk wasu hanyoyi domin kwantar mata da hankali duk da cewa nima hankalin nawa a tashe yake domin tsakanina da Mahaifinku babu daɗi , nema yake ƙarfi da yaji ya raba Rahima da gidan sa wanda nasan zugar 'yan uwansa ne da ni kuma ko kusa bazan lamunta ba , idan Rahima ta bar wajena ina zata ?? "har zuwa safiyar wata rana da na wayi gari Rahima kin yi gaban kan ki wajen barin Rayuwata , kin tafi kin barni cikin tashin hankalin da ya tunkuɗo min da naƙuda , "kika tafi ba tare da kin yi tunanin me hakan zai haifar ba cikin rayuwata , "duk wani wajen da nake tunanin zaki je Rahima naje neman ki har ms da wuraren da baza ki ba naje neman ki , " a cikin halin nan na matuƙar tashin hankali na haifi jaririyata da tun lokacin da na haife ta na shaidawa mahaifinku sunan ta Rahimatullah . " da ɗanyen jego na dunga fita kusufa-kusufa neman ki da hakan ya tunzuro Al-Mustapha yace muddin na sake fita neman ki da kaina a bakin auren mu , " a wannan ranar nima zuciyata a taurare take da zafin rashin ki dan haka nima na taso masa , a take a wajen na nemi da ya sawwaƙe min auren sa tun a nan domin kuwa fita neman ki yanzu na fara har sai ranar da na ganki , "shima da alokacin yake ganin zallar laifin ki na cewar ai ke da kan ki kika ga damar tafiya dan haka zaki dawo , "a fusace a wajen ya datse igiyar auren mu ba tare da yayi la'akari da irin raunin dake tare da ni ba , "Ban kwana a gidan ba na tafi tare da jaririya Rahima , na bar masa Hafsa da Zainab Hamza kuma yana makaranta, " nayi neman ki Rahimatullah har N'Djamena naje an tabbatar min da baki zo ba ƙarin tashin hankalina shine duk sauran ƙannena a cikin matsanancin talauci suke , " Na tattara musu duk wasu 'yan kuɗaɗen da na tafi da su na basu , na sake dawowa Nigeria , tare da taimakon ƙawayena biyu Hajiya Hadiza da Hajiya yaana , na sayar da tarin sarƙoƙi da ƴan kunnayena zuwa wara-waren zinare da nake da su , na sayi gidannan da muke ciki , na ɗora neman ki daga inda na tsaya saboda na tabbatar kina Nigeria wataƙila gari kika sauya , meyasa kika min haka Rahima ????  "aina kika rayu ? Ina mijinki kina da wasu 'ya'ya ne bayan wannan na cinyar ki ? Idan kina da su suna ina ?? Amnee ta ƙarasa bada labarin rayuwarsu da ɗora tambaya ga Khaalty Rahima wacce idanun ta yayi jazir tsabar kuka , Tausayin yayarta ya cinye zuciyar ta , ashe haka ta shiga damuwa akan rashin ta ?? ƙasa take son sharewa tayi rubutu , Amnee ta miƙe ta kawo mata takarda da biro , ta sanya hannu biyu ta karɓa , taƙaitatcen rubutu tayi a jikin takardar , " tsoron kar na zama sanadin rabuwar auren ku da Yaya mustapha yasa na tafi daga gareku ukhtee Amina ki yafe min , bansan ba zan zama sanadin tarwatsewar jin daɗin rayuwar ku . "Mairambiri shine sunan ƙauyen da na rayu tsawon lokaci a cikin sa kafin zuwan yan tawayen boko haram su tarwatsa garin su kashe mijina da manyan yarana biyu mata da suma nake zaton sun mutu , Amina da Fatima shekaru shida yanzu da mutuwar su .bayan su ina da wata 'ya da ita ma harsashi ya same ta ta mutu , a yanzu Bulama shine kaɗai ɗana . ASSALAMU ALAIKUM 'Yan uwa ina miƙo saƙon gaisuwata tare da fatan Alheri gare ku baki ɗaya , ina kuma mai yabawa bisa ga yadda kuke nuna ƙaunar ku ga littafin nan , nagode . [11/15, 11:03 PM] +234 806 600 1491: MAFARI ( Hargitsin Rayuwa ) Umm'muaz 39 Duk yadda Falmata take tunanin daɗin dake ga mallakar idanu ta tadda shi ya wuce haka , jin kanta take tamkar sabuwar halitta , Har bata so bacci ya shiga tsakanin ta da ganin hasken duniya , karambani kuwa babu irin wanda bata yi , har girki take karambanin yi Yousssouf kuwa yana taya ta , Shima a ɓangarensa baya gajiya da duk wasu tambayoyi da ko karambanin da zata yi , wani irin son ta yake yana riritata , Mama da kanta tasan cewa yanzu Mamarta ta samu waraka saboda wata kulawa na musamman da idanun ta sun hango mata wani ɗan datti a jikin kayan Mama zata yi maza ta gyara ta ta sauya mata wani , A kullum ta Allah sai ta miƙa godiyar ta ga Youssouf kamar yadda cikin duk wasu sallolinta sai ta ƙara godewa Allah akan wannan babbar kyauta da ya yi mata na dawo mata da ganin ta , Godiyar da take yiwa Youssouf ba a fatar baki kaɗai ta tsaya ba , har a aikace take gwada masa ta yadda take nuna masa ƙauna tare da ɗaukar buƙatun sa ba tare da gajiyawa ko ƙorafi ba . Kamar yadda likita yace tana cigaba da zuwa ana dubata , babu wata sabuwar matsalar da ta ɓullo tunda aka yi mata aiki . Idan tana da wata damuwa to ta lafiyar Mama ce wacce kwana biyu ciwon ta yake ƙoƙarin tasowa suna danne shi da tarin magunguna gami da ƙara ƙaimi wajen kulawa da ita , amma duk da haka kallo ɗaya za'a mata a iya hango tarin raunin dake tare da ita tun daga cikin raunanan idanunta da suka ɗan sauya launi zuwa ruwan ɗorawa har zuwa ƙafafunta da hannayenta da suka ɗashe suke yawan ɗaukar sanyi , Gaba ɗaya Falmata da shi kansa Biyamuradi Youssouf basa tare da walwala sosai , "Baban Mama ko dai za'a sake komawa asibitin nan ne maganar aikin Mama , Youssouf wanda yake shafa kan Mama wacce take kwance cikin jikin sa lamo , ya ɗago kan sa yana duban idanun Falmata da suke nuni ƙarara da damuwar da ruhin ta ke ciki , "Fatima duk wassu bayanai da zamu sake samu daga Doctora basu wucce batun baya da sunka faɗi muna , wanda kouma mun bar Lamari ga Allah zouwa lokacin da za'a samu damar yin aikin , Shiru tayi tana cigaba da kallon sa , cike da damuwa , so take yayi wani yunƙuri kome ƙanƙantar sa , Ji yayi gangar jikinsa na karban sakon dake fitowa daga cikin ƙwarar idanunta masu kyaun kallo , "idanun ki suna da kyau idan kina kallon Mutum da su Fatima , lokacin da basu da Lafiya kyan su bai kai haka bayyana ba , kina da sassanyan kallo Mai cike da nutsuwa , Murmushi tayi kaɗan , kafin ta ƙira sunan sa , "Baban Mama , Sai kuma tayi shiru , Kamo hannunta da yake kusa da shi yayi ya riƙe , "Ummh ina jinki menene ? " daman nace ko zamu je ni ɗin a gwada ni  ? "gwaji Fatima wanne irin gwaji , akwai damuwa ne ga lafiyar jikin ki ? Sunkui da kan ta ta sake yi tana jin nawin zancen akan harshen ta , sai dai tana jin zata iya yin kome domin ganin Mama ta samu lafiya , muryar ta a ciki tace , "ko Allah zai sa a dace un-un ko wai a jikina akwai abunda da za'a iya amfani da shi wajen yiwa Mama maganin , Kiris ya rage Biyamuradi Youssouf ya kwashe da dariya , sai dai ya gintse saboda yana son jaan ta , " Fatima kin manta likita yace ke baki iya bada jinin ki ? Cikin sauri ta katse shi , " ai ba jini na ba , wai a auna ko akwai cikin ? " ciki aina ? Yace da dariya a cikin sautin sa, Ɗago kanta tayi tana iya hango hasken haƙoransa da yake dariya, " un-un a jikina ko ? Dariya ya kwashe da ita , cikin ransa  ƙaunar ta na sake yawaita , kunya da kawaicinta yana burge shi haɗi da salon rashin wayewarta da baya sa ta fidda tsagoron ƙauyencin ta . "Fatima ciki ai sai ya nuna Alamunsa tukun ake zouwa ayi gwaji , hakanan bai yiwuwa aje ga gwajji sai a mouna dariya , Shiru Falmata tayi tana ganin wautar kan ta , to ita ya zata yi ne ? Ta matsu Mama ta warke ta samu lafiya kamar sauran Yara , tsintar kanta tayi da addu'ar Allah ya nufe ta da samun ciki nan kurkusa domin lafiyar Mama , Daren ranar basu samu bacci ba saboda jikin Mama da ya tsananta idan banda nishe-nishe da ƙananun kuka babu abunda take yi , hankalinsu baki ɗaya a tashe , Falmata ta rungume ta anjima Youssouf ya ɗauke ta ya ɗora a jikinsa , haka suka yi ta fama . Asubar farko a cikin tsananin sanyi suka nufi asibiti a take likitocin ta suka shiga bata kulawa , Ba'a fi awa guda ba ciwon ya lafa ta samu bacci , tana rungume a jikin Falmata Ƙarar wayar sa ya sanya shi miƙewa daga kujerar da yake zaune ya ɗan taka zuwa wajen ɗakin yana ɗaga ƙiran da ake masa wanda yake daga Tafeeda , " Youssoufa akwai Al'amari maigirma da muni da yake tunkaro ka , Sune kalaman da Yaji Tafeeda ya furta masa ba tare da sun ko gaisa ba , Ji yayi ya cigaba da cewa , "Bayan tsawon shekarun da ka kwashe kana ɓoye kuskuren da ka aikata yanzu kome yana daf da bayyanuwa batare da ka farga ba mutanen da suka ɗau lokaci suna bibiyar sawun duk wani motsi naka ba tare da ka kai ga hankalta ba gaf suke da cimma nasara akan ka , "Ya zama dole ku dawo tare da kai da 'yar taka da matar da ka aurawa kan ka kafin kome ya lalace , mafi girman lamarin shine nan da kowanne lokaci Maimartaba tare da Hajiya umma zuwa kan iyalai tare da 'yan uwanka zasu iya sanin Mummunar Fuskar ka , " Maƙiya kuma zasu samu damar kassara ka , wanda kafi kowa sanin me hakan ke nufi ?? "Ta-Tafeeda , meke Faruwa ne yi gaugawar sanar min , "ni a matsayina na 'dan ouwa a gareka zan yi dukkanin bakin ƙokarina wajen ganin lamura basu munana fiye da ƙima ba , duk kuwa da cewa ni ai ba bakin koume nake gareka ba , Ɗut-ɗut ! Yaji ƙarar Alamun yankewar ƙiran Tashin hankalin da ya zo masa a lokacin maigirma ne , me Tafeeda duk ya faɗa masa ?? "Tayaya ya san cewa tare yake da Fatima da Mama ?  "Su waye maƙiyansa masu bibiyar rayuwar sa ? "Fallasuwar Asirinsa a gurin iyayensa hakan na nufin ɗebe ƙaunar sa daga zukatan su , "wai shin me yake shirin faruwa ko kuwa ya ma riga ya faru  ?? Ya zama dole ya koma gida , Da sauri ya shiga neman layin Tafeeda sai dai har ta gama ƙara bai ɗauka ba , ya sake gwada ƙira a karo na biyu nan ma ba'a ɗauka ba , Tashin hankalin sa ya yawaita da har Falmata ma ta kai ga Fahimta , damuwar sa ta ƙara mata damuwa , sau biyu tana tambayar sa ko me yake damunsa ? Yana ce mata ba kome . Kafin dare Mama ta warware dan haka suka koma gida , "Falmata ta haɗa ruwa mai zafi ta yiwa Mama wanka ta shirya ta cikin jibga-jibgan kayan sanyi , kasantuwar cikin magunguna da Alluran da aka yi mata akwai masu sa bacci bata jima ba bacci ya sake ɗauketa , Itama wankan tayi ta shirya cikin wondo wide-leg da Rigar sanyi ribbed sweater ta ɗaura hular sanyi akanta , Ta fito ta cimma masa yana zaune a ƙasa ya jingina bayan sa da kujera , hannun sa biyu tallafe da ƙeyarsa , Babu wadatar haske a falon saboda duhun dare da ya shigo fitilar falon kuma ɗaya ce a kunne , kasantuwar idanun nata ba gani suke sosai ba , ya sa bata ma kai ga ganin sa a wajen ba sai duhu-duhu take gani , "Fatima , Ya ƙira sunan ta lokacin da ya ga ta kashe ƙafa daga ƙofar ɗakin , alamun tana buƙatar ɗan jagora , "zo nan , Yace da ita Inda take iya hango duhun sa ta nufa a hankali , kallo yake bin ta da shi ganin yadda kayan suka karɓi jikinta musamman ɗan wondon da bai kai ga sauka ƙasa ba , daga ƙungunta ya zauna ɗas saboda ɗaura shi da tayi akan rigar . Hannun ta ya kama ya ƙarasa zaunar da ita akan jikinsa yana jin yadda ƙamshin daddaɗan turaren da ta fesa yana ratsa hancin sa , Lamo tayi a jikin sa tana jin damuwar rashin walwalar sa na damun ta , " Alhamdulillah Mama ta samu sauƙi ko ? Tace da shi da dabarar son jin maƙasudin damuwar sa , "Mama ta samu sauƙi Alhamdulillah , Ya ce yana ƙanƙameta a jikin sa , "Har hankalin mu ya kwanta , bana son ciwon Mama ina tausayinta , "Fatima zamou kassance cikin shiri zouwa wassu kwanaki nan gaba zamou koma gida , " ɗago kanta tayi da son ganin fuskar ko Allah zai sa ta fahimci damuwar sa , "Baban Mama na ɗauka sai an samu lafiyar Mama ? Zai yi Magana wayar sa tayi ƙara , Ganin sunan Hajiya Umma a fuskar wayar ya sa zuciyar sa tsinkewa , Da sallama ya ɗau wayar , sai dai yadda ya ji ta amsa masa ya sa jin hankalinsa ya sake tashi , Sama-sama ta amsa gaisuwar sa , bayan nan abunda ta sanar da shi shine kawai duk me yake ya nemi izni ya taho gida cikin kwanakin nan kusa . Shiru yayi bayan ya ajiye wayar , tabbas akwai abunda ke wakana game da shi a gida . "Baban Mama... Ya katse hanzarin ta "Fatima zamou kouma gida , a gaba zamou dawo neman lafiyar Mama , Sai ta mayar da kan ta jikin sa tayi shiru , baki ɗaya walwalar da ta ɗan samu na murnar samun sauƙin Mama ta kau , Daren ranar babu wani armashi agare su musamman ma Falmata da damuwar da take ciki ta haifar mata da zazzaɓi da ɗan ciwon kai , dan haka washegari ta tashi haka sukuku , Karin kumallo ma sama-sama suka yi , Bayan sun gama karin kumallo su dukkanin su biyun sun yi shiru sai mama ce take ɗan wasan ta , " J'ai réservé notre vol, nous rentrerons à la maison le 18 le mois prochain , ( nayi mana tanadin jirgin komawa , zamu tafi ranar sha takwas ga watan gobe , ) Muryar sa ratso shirun wajen , "Allah ya kaimu Baban Mama , ko zaka sanarwar da Hajja itama ta fara shiri ko ? "Eh zan sanar da ita idan ya ragge kwanaki goma mu tafi sai tayi shiru cikin kwanaki biyar , idan ya rage kwanaki biyar da tafiyar mu sai direba ya ɗaukota daga Nigeria , "To Allah ya kaimu , **** Wasa gaske cikin 'Yan kwanakin Youssouf ya gaza samun kwanciyar hankali tsoro ne cike taf a ransa , duk kuwa da cewa babu wanda ya sake neman sa kan wani batu sai dai yana tsoro ne kar ko tana ƙasa tana dabo . Falmata har ta gaji da tambayar sa akan yadda ya zama koyaushe cikin tunani babu nutsuwar kirki , 'yar soyayyar da yake gwada mata mai sanyi da shiga zuci duk ya rage a wasu lokutan ma raba dare yake tunani , da juye-juye , Kasantuwar daman ita mace ce marar hayaniya mai kammalewa sai bata tsananta shisshige masa ba ta ɗan janye jikinta itama ta maida hankalinta baki ɗaya kan Mama , da kuma fama da kanta da take yi saboda wani ciwon kai marar daɗi da yake addabar ta tare da bugun zuciya fiye da ƙima duk tayi wata 'yar hidima sai ta ji mummunar gajiya da bugun numfashi sun taso mata , Mama da kanta ta san cewa Babanta ya rage kula da dararrakin ta sosai saboda duk ta dame shi zai samu ya zameta ya shiga ɗaki ya rufe , Ya rage sati biyu tafiyar su da ya ke tsawon kwanaki kusan goma da yin wayar sa da Tafeeda , wanda duk yadda ya so ya samu damar da zasu sake yin wata magana , Tafeedan yaƙi ba shi haɗin kai idan ya ƙira wayar sa ba bai ɗauka saƙonnin sa kuwa ya tura su babu adadi ta kan yanar gizo da kai tsaye ta hanyar saƙon karta kwana , nan ma ga shaidar an karanta sako amma babu amsa , dan haka shima ya zuciya ya daina neman sa . Ya fito wanka da safe ya tarar da miss call ɗin Tafeeda , da hanzari ya ɗau wayar bai ko tsaya shafa mai ya sanya kaya ba ya ɗau wayar ya shiga neman layin sa , Sai dai kakarun Amai da ya jiyo daga Falon su ya sanya shi sauƙe wayar daga kunnen sa ba tare da ya kashe wayar ba ya fito falon hankalinsa a tashe ya ƙaraso ga Falmata wacce take durƙushe daga ƙofar kitchen ɗin su tana Amai , Da hanzari ya ƙaraso wajen ya riƙo ta zuwa jikin sa bayan ya ajiye wayar sa a ƙasa da aka riga aka ɗaga kiran daga ɗaya ɓangaren ba tare da ya sani ba , "qu'est-ce qui ne va pas avec toi chérie, es-tu malade? ( me yake damun ki ? Baki da lafiya ne ? ) Bata amsa ba illa yunƙurin Aman da ta cigaba da yi duk kuwa da babu kome a cikin nata , Shafa bayanta ya shiga yi yana ɗan bubbugawa tare da jero mata sannu , Mama wacce tashin ta kenan daga bacci ta jiyo muryar su ta fito , itama ta tsaya tana kallon su fuskar  ɗauke da alhini da 'yar muryar tace "Papa qu'est-ce qui ne va pas avec Mamma ? "Princess Maman ki bata da lafiya ne, dauko min papier mouchoir dagga ɗaki na goge mata baki , "To , Ta juya da ɗan gudu zuwa ɗakin su , "Sannu Fatima , Yace cike da tausayawa ,  Daga can ɓangaren Hawaye masu ɗumi suka silmiyo daga idanun Hajiya Umma , ta zare wayar Tafeeda daga kunnen ta tare da miƙa masa wayar , Karɓar wayar yayi ya duba wayar yaga ba'a katse ta ba dan haka cike da tashin hankali ya kara a kunnen sa yana fargabar ko wani abu ne ya faru da Youssouf ɗin , Sai dai ya ƙarashi Maganar sa bai ji Youssouf ɗin ya amsa ba , sai muryar wata mace yake ji ƙasa-ƙasa , dan haka ya katse wayar waigo ga Hajiya Umma , "Umma Lafiya Yarima yake kou ? "babu shakka lafiya yake , ta amsa da wata irin murya , Ganin yanayin ta ya sa Tafeeda miƙewa yayi mata sallama zuciyar sa cike da tunanin meye haka Youssouf ya faɗi wanda ya sa Hajiya Umma ƙwalla ? Shi daman zouwa yayi ya gaishe ta tare da cigaba da kwantar mata da hankali bayan tashin hankalin da ta shiga a kwanaki sakamakon wani Al'amari mai girma da ya taso game da Youssouf ɗin , wanda shi yayi tsayuwar daka wajen ganin lamarin ya dai-daita da a yanzu yake mataki na ƙarshe na gyara kome wanda kuwa hakan ba zai samu ba sai da haɗin kan Youssouf ɗin , tunanin ko zai yadda da lamarin da zai je masa da shi a matsayin shawara ko ba zai yadda ba ya sanya shi yin jinkiri yana nazari dan haka nema yaƙi yarda suyi magana da Youssouf ɗin Sai fa yau da Hajiya Umma ta sa ya ƙira sa a gabanta ta warware masa labarin mummunan ƙullin da aka so yi masa , Sai kuma ya ga Umma ta ƙare wayar ba tare da ta ce kome ba sai ƙwalla , lamarin da ya ƙulle masa kai kenan , koma menene zai ƙira Youssouf ɗin ya ji . A ɓangaren Su Youssouf bayan Falmata ta gama Amai ya gyara wajen ya ɗau wayarsa bai lura da Shaidar an ɗaga ƙiransa ba saboda hankalinsa da yake kan Falmata wacce sai numfarfashi take saboda ƙaruwar bugun zuciyar ta tare da ciwon kai da ya haɗu mata , Ko sannu da Youssouf yake yi mata da kyar take amsawa , "Fatima ko mu tahi hospitalisé ne ? Jikin ta babu kuzari ta gyada kai , Cikin hanzari ya shiga ya shirya ya wankewa Mama jiki tare da goge mata baki , ya dawo ya tarar da ita tana baccin zomo , "Fatima mu je ki shirya , Shi da kansa ya taya ta ta gyara jikinta yana riƙe da hannun ta suka fito " za ki iya tafiya da kan ki ko kuwa na ƙira taxi , "zan iya tafiya , Basu sha wata wahala ba kasantuwar daman tana kan ziyartar likita , dan haka suka samu ganin likitan ta inda shi kuma bayan tambayoyin da yayi mata da duk bayanan da ta ba shi , ya miƙa su ga wata likita daban , wacce ta sake yi mata tambayoyi , Daga haka ta yi mata gwaji , bayan bayyanar sakamako , da fara'a likitar take miƙa musu sakon taya murnar cewa Falmata tana ɗauke da ciki na tsawon sati huɗu , Duk da cewa Falmata tana jin yaren faransanci babu laifi , Amma a yau ji tayi sam bata Fahimci me likitar ke nufi ba , tamkar ta manta ma'anar kalmar , Sai da ta ga Biyamuradi Youssouf ya rungume ta , yana bayyana farin-cikin sa da lokaci guda Albishirin da likitar tayi masa ya wanke masa zuciya tare da yin awun gaba da duk wata damuwa tasa , "Ya'ya ai arziƙi ne . "Fatima Tu es enceinte, tu portes mon bébé , Alhamdulillah Ya ɗago fuskar ta ya sumbanci goshin ta , Hannunta ta kai kan nasa hannun da yake tallafe da kumatun ta , kyawawan idanun ta na bayyana farin-cikin dake maƙare da zuciyar da "Baban Mama da gaske ina da ciki ? Zan haifi jariri daga cikina Mama Zata samu dan uwa , Mama zata wa.... Katse ta yayi ta hanya ɗora laɓɓansa akan nata ya sumbace ta , "Mama da Yumna zasu samu ɗan ouwa ko ƴar ouwa insha Allah nayi Farin-ciki Fatima . Mama da take tsaye tana kallon su ba tare da ta san me suke yiwa murna ba , sai ita ma ta sa dariya ta taho ta rungumo su , Hannuwansa ya sa ya zagaye a jikinsa yana jin waɗannan rayukan guda biyu sun zama wani ɓangare na daga rayuwar sa , Da wannan farin-cikin me tarin yawa suka baro asibitin zuwa gida , bayan likita ta basu shawarwari tare da  'yan magungunan da zasu taimaka a matakin farko na zaman ciki . Falmata Ji take babu wata rana da take kai wannan ranar farin-ciki a wajen ta , minti kaɗan zata kai hannu ta shafi cikin ta , farin-cikin ta biyu ne , Tana ganin cewa lokacin warkewar Mama yayi tunda gata ɗauke da ciki , Da shigowarsu gida wayar sa tayi ƙara  Tafeeda ne ya sake ƙiran farin-cikin sa bai ɓuya ba a muryar sa suka gaisa da Tafeeda , Kafin Tafeeda ya ɗora da cewa , "Yarima magana nake so muyi kou ka bani dama ? Jin haka sai ya miƙe daga jikin Falmata ya fita zuwa 'yar barandar gaban gidan , "ɗan ouwa na baka dama faɗi ina jin ka , Yace masa a taƙaice , "Magana ce zamu yi game da lamarin yarinyar nan da kake boyen sa gareni tsawon wannan shekaru , na riga nasan koume kan zaman ka tare da su da amren innan ita yarinyar da kake har gidan da kun ka tare a Niamey na shina Yarima , "To munin Al'amarin ba dagga gareni yake ba , sai fa dagga maƙiya waɗanda sunka dunga bin lamarinka , a cikin binciken da nai kai tamkar da sanya hannun su kome da ya faru ya kai ga faruwa  , "Lamari ya munana ta inda zance ya taho ga Fada ya iske kunnen Maimartaba da Hajiya Umma bai tsaya nan ba har sai da ya iske mutanen cikin Fada baki ɗai ba'a kouma san waye ya fiddo maganar ba , "cewa Yariman Maraɗi yana da ɗiyar banza bata Amre ba , tare da yin zaman banza da Mahaifiyar ta zaman dadiro , tun dagga Nigeria , "Yarima nayi duk bakin ƙoƙarina wajen ganin anbi daddigin masu yaɗa maganar nan an dakile bazuwar ta , kouma anyi nasara ,sannan na ƙaryata batun gaban moutanen cikin fada tare da Maimartaba , "Amma nasan wannan yunƙuri nawa ai bai isa ba ya kawo ƙarshen maganar nan tunda kouwa akwai ta da gaskiya , maƙiya ba za su bar lamarin nan ba . "Menene mafita a yanzou ? Youssouf ya katse dogon bayanin da Tafeeda ke yi masa ,cikin miƙa wuya 'Mafita gouda ce ,ka rabu da ita wannan yarinyar da kake amre , ka sallame su su tafi tare da ɗiyar nan , "ka rabou da ita domin tsarkake kan ka dagga zargin al'umma ,tare da aibatawa , "ka rabou da ita domin tsira da mutuncin tare da ƙimar ka , "ka rabou da ita doumin gujewa russa alaƙar ka da iyaye da 'yan ouwan ka , "ka rabou da ita doumin gujewa samar da bakin-ciki a zuciyar Mahaifiyar ka , "ka rabou da ita domin gudun samun galabar maƙiya a kan ka , "ka rabou da ita domin tsarkake masarautar ku tare da kaiwa ga matakin nasarar zama sarkin maraɗi a watarana . "ka nesanta kan ka daga wannan ɗiya da innarta doumin tsallake ramin maƙiya , muddin ka ƙiya ? Za ka gamou da dariyar maƙiya da baƙin-cikin iyayen ka . "cigaba da zama da itta yana nufin rassa kowa tare da kai ciki kouwa har da ni kaina . "Tafeeda , Youssouf ya ƙira shi da wata irin murya mai cike da tashin hankali , "Yarima shawara ce ni na baka zaɓi yana dagga gare ka , ni na barka lafiya , Wani iri yake ji tamkar an zare masa laka , menene yake shirin Faruwa da rayuwarsa ne ? Kalmar Rabuwa da Fatima tayi masa nawin saurara ko a kunne kawai , To amma kuma shi ya zai yi ne? Ji yake kamar an raɓa ƙwaƙwalwarsa da duk wata tunani . Cigaba yayi da tsayuwa a wajen ya gaza motsawa Hannuwan ta ya ji sun ratsa kirjin sa daga bayan sa ta rungume shi , tare da kwantar da kan ta a bayan sa , Cikin sanyin muryar ta tace "Baban Mama tun ɗazu nake jiran ka , kazo muyi Sallah mu godewa Allah , akan wannan babban arziƙi da ya bamu . Hannu ya kai ya zagayo da ita ta gaban shi , Kallon fuskarta da take ɗauke da tsantsar farin-ciki yayi , suɓul da ita sai ƙyalli take tare da wani irin haske na musamman da ta ƙara a 'yan kwanakin nan, Ji yayi tsikar jikinsa ta tashi dawowar kalaman Tafeeda cikin kunnuwan sa yasa jinin jikin sa tsinkewa , "Fatima ina son ki dayawa , je t'aime tellement Fatima Yace da wata irin murya lokacin da yake rungumeta tsam a jikin sa , yana fidda ajiyar zuciya a zahiri . Ji tayi riƙon da yayi mata yayi tsanani da kyar take fidda numfashi  , dan haka ta motsa da kyar , "Baban Mama mu shiga ciki na zauna , Tana jikinsa suka taka zuwa cikin gidan ya zaunar da ita akan kujera , amma shi ya gagara zaman saboda tashin hankalin da yake ciki , "Baban Mama ... "Fatima ku zauna a gida ke da Mama ku jiraye ni zan fita na sayo mana abubuwan buƙatu kadan yanzu nake dawouwa da gaugawa ba zan daɗe ba kin ji kou ? A sanyaye ta amsa da "to , tana gyaɗa kai , Daga haka ya juya ya fita , ba tare da ya san inda zai tafi ba , kawai so yake ya zama shi kaɗai bai san ɗanɗanon shakuɗuwar farin-ciki da baƙin-ciki a lokaci guda ba sai yau , Bai san girma da tsoron da yake cikin rasa abunda kake so ba sai yau da layi yake shirin shatuwa tsakanin sa da abubuwa biyu mafiya soyuwa agare shi , Bai san da irin wannan tashin hankalin da yake sa ɗimuwa ba sai da ya tsinci kan sa can nesa da unguwar da yake ba tare da ya sani ba , Tsayuwa yayi a ƙarƙashin Doguwar bishiyar (Pinus taeda) da duk ganyayyakin ta suka gama zubewa saboda sanyi , Hannun sa ya zira a aljihun rigar sanyin jikin sa cikin rashin sanin makomar rayuwar sa , Waye zai tallafa masa ya fahimce shi ? Tayaya zai yi bayani a fahimce shi cewa kome da ya faru gare shi ya faru ne bisa ruɗin shaidan da kaddara maigirma , kaddarar haihuwar Mama da Auren Fatima ? Waye zai faɗawa ya saurare shi cewa Fatima ta riga ta zama mahaɗi na cikamakin farin-cikin rayuwar sa ? Mama ɗiya ce jini daga cikin jinin jikin sa dake gudana ,ta yaya zai iya tsame ƙwayar jinin sa daga jikin sa ? " daga gefe ya hango wani brewery ( wajen sayar da giya ) ya tsallaka ya shiga wajen ya zauna , akan ɗaya daga cikin kujerun gurin , ɗaya daga cikin ma'aikatan wajen ta zo da tare da gaishe shi , Kan sa yana kallon teburin gaban sa ya ce mata Please bring a bottle . bata tafi ba ta fara lissafo masa sunayen giyar da suke da ita, ya katse ta ,   Bud Light Bata jima da sai gata ɗauke da kwalbar giyar da ya buƙata da ɗan kofin gilashi , tare da farfasassun ƙanƙara cikin wani ɗan mazubi na gilashi . Tsirawa kwalbar ido yayi yana jin ƙaruwar damuwar sa da yake zaton idan ya kurɓa giyar zata gusar masa da wannan damuwar , da rabon sa ya sha ya kai wasu shekaru , Ɓincine bakin yayi ya tsiyaya a kofin , tunani ya shiga yi irin nacin addu'a da ya dunga yi akan Allah ya nufe shi da daina shan giya , da ƙarfin addu'a da tirjiyar da yake yiwa shaidan aduk lokacin da ya ji jarabar son shan giyar, ya samu nasarar daina sha sam Yau sanadin damuwar da giyar ce ta zama sanadin faɗawar sa domin ita ce sanadin kome gata a hannun sa yana son sake sha , wataƙila masifar da zata iya sake jefa shi ciki sai yafi wanda yake ciki s yanzu Ajiye kofin yayi ya miƙe zumbur ! tamkar ya ga abun tsoro , istigfar ya shiga yi a zuciyar sa , Da hanzari ya zaro kuɗaɗen da bai san adadin su ba ya ajiye akan teburin ya kama hanyar barin shagon , zuciyar sa na tsananta bugawa , Ya kama hanyar komawa gida yana sake zurfafa a tunani ƙwarai yana buƙatar wani babba a cikin lamarin sa da Fatima , waye zai tintiɓa ? Hajja , ita tafi kowa kusanci da Fatima a halin yanzu , yana buƙatar suyi magana shi da ita , ko ita zata fahimce shi ? Wayar sa ya zaro daga aljihu ya shiga neman layinta , ƙira ɗaya-biyu ta ɗauka suka gaisa , tana tambayar sa su Falmata da Mama ? Ya amsa mata da duk suna lafiya , sai kuma ya gaza fayyace mata cikin sa kamar yadda yayi niyya to ta ina zai fara ƙiran kan sa da mazinaci ? Kai bafa zai iya ba  "Hajja ki fara shiri idan Allah ya kaimou nan da sati mai zuwa direba zai zou ku taho Niger mouna dawowa nan da kwanaki goma sha huɗu Daga ɓangaren Hajja ta amsa da murnar jin zasu dawo ta san an samu nasarar abunda aka je nema kenan . "Babu kome Babban soja zan yi shiri kafin ranar nayi sallama da yan uwa , "Nagode Hajja , zai zo miki da sakon da za ki bawa dangi ki kuma sayi abun buƙatar da kike so kafin ku taso , "Har da wahala kuma Haba ? To madallah nagode , nagode Babban soja , Suka yi sallama ta ajiye wayar , Yakaka wacce tare suke da hajja a kitchen suna hidimar girkin dare,  da duk hankalin ta ke kan zancen Hajja da ta ji tace zata tafi , ta ɗan matso kusa da ita , "Hajja tafiya ce ta kama ki ne ? A kaikaice Hajja ta dube ta kafin ta cigaba da kaɗa miyar da take yi , "Eh Uwarɗakina Falmata ce zasu dawo daga Amurka , zan koma cikin sati mai kamawa ,  na gyara gidan kafin su iso , "Hajja nima zan je , zan biki na ga Falmata na , zan nemi izni wajen Baba . Ba tare da ta jira amsar da hajja zata bata ba ta fita da saurin gaske , zuciyar ta maƙare da tasowar binannen bakin-cikin ta , lokaci ya matso na raba tsakanin ƙanwar ta , tare da ƴar ta,  da wannan mugun mutumin , mayaudari . Assalamu alaikum , Da fatan duk kuna lafiya ? Nasan kun yi mamaki ko ? Haaaa , ina masu cewa sai wani watan zasu ga sabon update ?ha'aan kun ji kunya ko ? 😂 To ƙaƙa ƙara ƙaƙa ? Yau ina son jin ra'ayoyin ku pls , A gaskiya ghost readers sake bunƙasa kuke yi amma ba kome liti bad boy yana madakata shi da Hajja suna jiran ku 😂 Nagode . [11/23, 5:46 PM] +234 706 635 0638: MAFARI ( Hargitsin Rayuwa ) umm'muaz 40 Cikin sa'a da Yakaka ta nemi izni wajen Prof kan ta bi Hajja zuwa wajen 'yar uwarta sai Prof bai hana ta ba , sanin cewa da yayi haƙiƙa akwai buƙatar su ga juna ita da 'yar uwar ta  . Sai dai yayi mata jirwaye da kamar wanka , ya yi mata nasiha tare da jaan kunnen , a ƙarshe ya gindaya sharadin kar ta wuce kwanaki goma zuwa sati biyu a Niger ɗin ta dawo gida nan wajen sa , Cike da ɗokin sake ɗaura idanunta akan Halittun biyu mafiya soyuwa agareta ta fara shiri, duk wasu 'yan kuɗaɗen da take da su irin wanda Prof yake ba ta da wanda Rahima ke mata kyautar su da suka tasamma dubu goma sha biyar duk ta tattara su ta ƙulle ta nufi kasuwa , Sayayya ta shiga yi gefe guda na zuciyar ta na cigaba da saƙe-saƙen irin mummunan matakin da zata ɗauka akan Youssouf , Daga Jiya zuwa yau,  iyakar tunanin ta kan matakin da take ji zata iya ɗauka ya ƙare ne akan kawai abu mafi sauƙi shine , Idan Har sun hadu zata ce da shi, ya saki ƙanwar ta ya kuma bata 'yar ta , ko kuwa ta kai lamarin gaban iyayen sa , waɗanda ta riga ta san ko su , su waye ? ta san cewa shi ɗan sarki ne tun a lokacin da Samy Baby ta goranta mata akan sa , Ta san wannan ce kaɗai madogarar ta , idan har ba haka ba ai ita bata isa jaa da shi ba . Tana da tabbacin ba zai yarda asirin da yake tsakanin sa da ita ya tonu ba da ta riga ta san ya ɓoyewa mutane dayawa ciki kuwa har da Falmata , ita kuma ta shirya sanar da ita gaskiyar kome da ya faru tsakanin su da Youssouf ɗin, ta tabbatar daga lokacin da Falmata ta san kome baza ta sake yarda da shi a matsayin Miji ba , za kuma ta taya ta su ƙwato Mama suyi dawowar su nan. Da tunanin hakan ta ƙaraso wajen sayar da Takalman mata da yara irin na roba masu sauƙin kuɗi , Tafi son ta saya musu 'yan kayan sanyawa a jiki musamman dayake bata san yaya rabuwar ta su da shi Mayaudarin zai kasance ba , wataƙila suyi irin rabuwar da yayi da ita a baya , watau ya yasar su akan titi babu ko suturun kirki ya kora su . Dan haka ya zama dole ta yi musu guzurin kaya daga Falmatan Har Mama . Daga wajen 'yan takalman inda ta ɗauka musu ƙafa bibbiyu duk da cewa kintata tayi ta auna girman ƙafafun su a tunanin ta , Sai ta nufi wajen 'yan kayan yara , nan ma ta auna da girman Mama da ta gani a hoto ta saya mata shiga biyu masu sauƙin kuɗi , Ƙaunar Falmata ga Ƙuli-ƙuli mai sugar , ta tuno dan haka ta je ta saya mata shi na ɗari uku fal cikin ƙaramar baƙar leda ta ɗaure , Ba zata yi wasa da kuɗin ba saboda guzuri sanin da tayi basu da inda zasu samu kuɗin mota a Niger idan suka yi rabuwar baram-baram da Youssouf . Ko da haka ta kasance wataƙila baza su shiga matsala mai yawa ba kuɗin hannun ta zai isa dawo da su Nigeria . ***** Kwanakin da suka biyo duk tayi su cikin ɗokin zuwan ranar tafiyar su ne ,  daga Rahima har Hajja sun fara gajiya da sabanbatun ɗakin da Yakaka take musu daga sun zauna . Ta ƙira Malama Maryam ma ta sanar da ita , inda ita ma dai Nasihar ce ta ɗora mata bayan ta mata addu'o'in kariya , daga nan ta ƙira Lubna wacce ta gama fushin ta har ta huce akan rashin zuwa auren ta da tayi , murna sosai Lubna ta yi mata tare da addu'ar dawowa Lafiya . Ta so ta je ta yiwa Amnee Sallama amma Amnee sun yi tafiya tun wajen sati uku da suka wuce ita da Ƙanwar ta Khaalty Rahima , Wacce aka ce ta dawo , duk da cewa bata samu damar ganin ta ba , amma tayi murna ƙwarai da dawowar ta , har ma tayi fatan ina dai su ma Allah zai dawo musu da Mamar su haka watarana ? Sai dai ta ji tausayin ta saboda yadda Rahima take bata labari ta sha wahalar rayuwa sosai har ta ƙurumce dan haka ne ma suka tafi jahar Lagos inda za ta ga wani Babban likitan kunne a wani shahararen asibitin cutar da ta shafi kunne zuwa maƙoro dake jahar Lagos ɗin , A yadda Rahima ta shaida mata daga zarar sun dawo , za su dawo nan gidan ne ita da Amnee baki ɗaya inshaAllah , Duk da bata san me ya raba Amne da gidan ba , amma tayi murna sosai da ta ji cewa zata dawo , saboda irin ƙaunar da take nuna mata , *** Babu irin gargaɗi a fakaice da Hajja bata yi mata ba , tare da hannun ka mai-sanda akan kar dai fa ta je da zummar ƙulla wani mugun abu. Har 'yar nasiha ta dunga yi mata akan ta rungumi kaddarar ta , ta haƙura Allah zai kawo mata wani Mijin Sai dai kasancewar ta ba mai yawan magana ba ya sa bata tankawa Hajja har ta yi ta gama zantukan ta da ta ɗauke su a sowar biri . Amma cikin ranta ta kan yi mamakin Hajja a lokuta da dama , ƙarfin halin ta kuma na bata haushi , wacece Hajja ? Yaushe ta shigo Rayuwar su ita da Falmata ? Shin wai zato take ta fi ta ƙaunar Falmata  ne ? Sai dai ta haƙura ta binne ɓacin ran ta har zuwa ranar da zata gwadawa Hajja cewa lalle ita da Falmata sune ɗaya . Kamar yadda suka shirya ana gobe ranar tafiyar su Direban da zai kai su ya iso da ƙarfe takwas na safe , saboda kwana da ya yi a garin damaturu Aka sauƙe sa tare da ba shi wajen kwana , a kuma ranar ne da hantsi misalin sha ɗaya na rana Zainab da Hafsa da 'ya'yan su har ma da Sofi suka iso dukkanin su daga garin Abuja , Nan take gidan ya daina yiwa Yakaka haske , ta shiga hidima da su da 'ya'yan su , ba ji ba gani . Ga daga Zainab ɗin har Hafsan basa wani sakar mata fuska , bare kuma Sofi wacce ko giftawa tayi ta gabanta sai ta bita da zagi da harara , duk ta bi ta takura ta gaza walwala , Rahima ma da take jin daɗin ta yau ta ga 'yan uwanta ta ƙule a cikin su , suna hirar su ta 'yan uwa , Cikin hirar da suke yi ne ta tsinci suna maganar isowar Amnee da khaalty Rahima da Doctor Hamza a gobe wanda shine ma maƙasuɗin zuwan su . Har ta juya zata fita a falon bayan ta durƙusa har ƙasa ta miƙawa Hafsa Feeding bottle ɗin jaririyar ta da ta wanke da ruwan zafi , ta tsinci Muryar Zainab tana ƙiran ta , "Ke , un wa ma kike da suna ? Ki zo zamu hau sama ki taya mu gyara , wallahi Hafsa dan dai kun ƙi ne amma ai da mun taho da munnira da indo masu aikina , da wannan uban aikin da zamu yi ,  ba gara mun biya musu kuɗin jirgin ba mun zo da su sun yi aikin , aikin fa ba na wasa bane duk ɗakunan saman nan uku da Falo sai mun wanke su mun gyara ,  Sofi ta katse ta , "To ba ga wannan balamar ba , meye amfanin ta da ba za tayi aikin ba ? Rahima ta katse ta tana ɓata rai  " a gaskiya Antie Safiyya Aikin nan ya yiwa Yakaka yawa kin kuwa ga yawan ƙurar da take sama ? Ɗayan ɗakin nan na gefe ni tun da nake ban taɓa ganin an buɗe shi ba , "mts kome yawan sa daga nan zuwa gobe ai zata gama ke baki san ƙauyawa horan aiki bane ? "gobe zata yi tafiya ki... "Auntie Zainab zan iya a nuna min wajen , Yakaka ta katse jayayyar da take neman ƙulluwa tsakanin Rahima da Sofi , " Rahima ki nuna mata ta fara aikin kafin mu zo , Ta ƙafar benen dake cikin Falon suka hau sama , Yakaka sau ɗaya ta taɓa hawa saman tun lokacin bikin Zainab sai fa yau , Bakin ta ɗauke da Bismillah ta ɗora da Sallama ta shiga Falon da yake ba kome sai tarin ƙura buɗu-buɗu da gidan gizo-gizo , hatta shimfiɗar carpet ɗin an naɗe su , "Yakaka ki ga fa aikin da Auntie Safiyya ke cewa zaki iya yi ke ɗaya  ? Ita dai muguwa ce wallahi . Rahima ta furta Hakan cike da jin haushi , Murmushi Yakaka tayi , lokacin da take sanya ƙasan hijabin ta ta ɗaure daga kan hancinta zuwa bakin ta , "zan yi iyakar Ƙarfina Rahima , Ta furta hakan lokacin da take sunkuyawa ta ɗau sabon abun cire yanar gizo-gizo da ta gani a jiye a ƙasa daga dukkan Alamu an tanade shi ne dan yin aikin , Da addu'o'i a bakin ta ta shiga aikin cire yanar gizo , ** Ba su suka gama aikin da mafi yawa Yakaka ce ƙarfin sa ba , sai kusan tara na dare , Iyakar gajiya Yakaka ta yi sa , duk jikinta ciwo yake musamman bayan ta saboda sunkuyon shara , ga ƙurar da ta shige mata hanci ta sa mata mura sai attishawa take yi . Washegari dakyar ta iya tashi tayi Sallar asuba ita da Hajja suka hau shiri , Banda mita babu abunda Hajja take yi "Ace wai Yaran mata da ku sai dai ku yi kwance shaɓe-shaɓe kuna jiran a girka a kawo muku ? Wallashi yau babu wacce zan yiwa hidimar girki , girkin Alhaji kawai zan yi ,  tafiya ce mai nisa a gabana , " Akwai sauran tuwon jiya shi zan ɗumama mana ni da ke da direba , shige mu  tafi kitchen ɗin ' kafin su gama baccin su ta shi mu mun yi nisa , kiyi abu da jikin ki Niger ba nan kusa ba gara mu kama hanya tun da duku-duku , Da sauri Yakaka ta ƙarasa sanya Hijabin ta , ta bi bayan Hajja zuwa kitchen , *** Ƙarfe takwas na safiyar Ranar Talata , Yakaka da Hajja tare da direban da zai kai su suka kama hanya , bayan sun yi Sallama da Prof ya musu fatan Alkhairi tare da basu Dubu biyar -biyar su ƙara a guzuri . Duk da cewa Yakaka ta yi tafiya mai ɗan nisa tsakanin Abuja da Maiduguri , amma ta riski nisan tafiyar tsakanin jahar Borno Nigeria  da Niamey Niger da tazarar da ta shallake tunanin ta , tun tana zaton an kusa lokacin da ta ga Yamma tayi rana ta faɗi , Har ma ta tambayi Hajja ko sun iso ? Hajja ta shaida mata ai yanzu ne ma zasu tsallaka boda zuwa ƙasar Niger , sai ta maida kanta ta kwantar a jikin kujera tana me cigaba da kallon rairayin saharar da ya tafi iya ganin ta da tsilla-tsillan bishiyoyi ,  Cikin ran ta tana sake jin haushin Youssouf da ya shata tazara mai tarin yawa haka tsakanin ta da ƙanwar ta , Ba su suka isa Niamey ba sai sulusin dare , ƙarfe biyu saura , kai tsaye direban ya dau hanyar gidan Youssouf  da su , Suka yi amfani da 'yan mukullin hannun shi direban suka shiga cikin gidan  A babban Falon gidan da yake sashin Falmata suka yada zango ,kasantuwar akwai gajiya Mai tarin yawa tare da su musamman Yakaka da har wani tsuku take ji jikinta na yi mata saboda gajiya, ga idanun ta da suke cike da bacci , Nan falon suka yi rashe-rashe ita da Hajja Bayan sun sallami direban ya yi tafiyar sa a daren , suka kulle gidan , Direban da ya kawo su yana juya kan motar kafin ya ɗau hanya sai da ya ɗau wayar sa ya ƙira wani layi abunda kawai yace shine , " Ranki ya daɗe na kawo su gidan, matar da take kula da ita tare da wata mace da cikin hirar su na fahimci 'yar uwa ce gare ta , Ya ɗan saurara kaɗan , kafin ya ɗora da cewa , "gobe ma zan dawo wajen su doumin jin ko suna da watta buƙata kamar yadda shi yace , "To ki huta Lafiya ranki ya daɗe . **** Washegari saboda gajiya basu farka da wuri ba sai kusan ƙarfe bakwai na safe sallah suka fara yi , kafin Yakaka wacce tayi jugum daga inda take zaune tana ƙarewa taffaɗan falon kallo da yake wadace da kayan more rayuwa irin na zamani , Ji tayi zuciyar ta ta ɗan rage zogi ganin kyakkyawan muhallin da Falmata da Mama suke rayuwa a ciki , Amma ko kusa ƙudurin ta na raba su da rayuwar gidan bai sauya ba , Ganin ta ta mayar kan Hajja wacce take addu'o'i ganin ta idar ya sa ta gaishe ta , Hajja ta amsa mata tana tambayar ta yaya kwanan baƙunta ? *** Kafin tara da rabi sun gama aikin gyara gidan da cikin sa bai wani cika datti ba sai ƙura da suka gog-goge , Hajja ta ɗaura musu girki ita kuma Yakaka ta fito sharar harabar gidan , Da kallo take ta bin Babbar ƙofar da take gefe tana fuskantar mai shigowa gidan wacce take da ƙofar gilashi , amma ba'a iya hango abunda ke ciki saboda tafka-tafkan labulen da suka rufe , Takawa tayi a hankali ta ƙarasa jikin ƙofar ta tsakanin labulen da bai kai ga haɗewa ya rufe ba take iya hango cikin Babban Falon , Ta ɗan sake matsawa jikin ƙofar ta sa fuskar ta sosai tana leƙen cikin falon da haka kawai ta damu da son ta ga menene a ciki ? Akan idanun ta ta ga giftawar Mutum a cikin falon , da ya sa tayi saurin ɗago fuskar ta lokaci guda tana tunanin aka ce kuma babu kowa a gidan sune ma suka buɗe gidan , kuma sun rufe tun cikin dare har kuma yanzu ma gidan a rufe yake to waye kuma ta gani ta cikin falon ko nan ɗin ba ɓangare bane na gidan ? Sake mayar da kan ta tayi tana leƙen cikin falon bata ga kowa ba , amma ta cigaba da yawata idanun ta a ciki har zuwa wani ɗan lokaci  kafin ta ji an dafa ta ta baya , A tsorace ta waiga , ganin Hajja ce a tsaye tana bin ta da wani jirkitatcen kallo , ya sa ta yin ajiyar zuciya , "Hajja akwai mutum a falon nan ko ? Wani kallon yatsu-tsu Hajja tayi mata , "akwai mutum fa kike tambayata 'yar nan ? Gidan mutane kya tambayeni ko da mutum ? Nan da kike gani sashin shi Maigidan ne Baban Mama , Mijin Falmata . "Amma kamar na ga fa mutum yana yawo a ciki Hajja ko shi ɗin yana nan ne ? "wa ya sani ko Fatalwar sa ce kika hango , saboda shi dai kam baya gari , sai dai in kuma binbinin sa kike a zuci  abunda ni dai nake so da ke ɗaya ne , " ki kama kan ki , saboda kin ga dai yanzu a matsayin sirikin ki yake , ke kuma a matsayin Fatalwa kike a wajen sa , "Dan haka ki kame ki dunga nuna halin surukutaka, ki manta da mu'amalar ku ta baya da ta riga ta shuɗe muddin kina son nuna dattaku ato . Jikin ta a sanyaye ta kama yin sharar da take da nufin yi , kalaman Hajja suna mata yawo a zuci , duk da ta sha  faɗa matan hakan yafi sau shurin masaƙi daga ranar da ta ƙudurci niyyar biyo ta , amma kalaman basu taɓa huda zuciyar ta irin na yanzu ba ko me yasa ? Ƙarfe goma direban da ya kawo su yazo , gaisawa kawai suka yi da Hajja tace yayi tafiyar sa anjima su da kan su zasu kasuwa , Ransa ya nuna ba haka ya so ba , amma ba yadda ya iya haka ya tafi yana muzurai . Rochester New York Tun bayan bayyanuwar cikin jikin Falmata laulayi ya sako ta gaba , laulayi take irin mai wahalarwa , kome ta ci amai take , ga kasala da rashin ƙarfin jiki , kusan kwance take yini , Youssouf ke yin kome na daga aikin gidan da bai cika yawa ba . Ga ranta da yake a dagule saboda batun komawar su gida , so tayi Mama ta warke kafin komawar su wacce cikin kwanakin nan jikin nata yake yawan matsanta mata . Sai dai duk yadda ta so Baban Mama da ya yarda ya ɗage komawar su gida saboda a yiwa Mama akai tunda ga damar ta samu , ita ta amince a yi amfani da jinin abunda ke cikin ta a yi Mama aiki , Amma yaƙi amincewa , hankalinsa yayi gida , har saɓani suka kusa samu a ƙarshe ya ce ba zai amince ba da abunda yake cikin ta da Mama duk ɗaya suke a wajen sa , hakkin su ne ya kare lafiyar su , su duk biyun ba zai yi abunda zai iya sa abunda ke cikin ta a hatsarin da zai salwanta ba , kamar yadda ba zai so rasa Mama ba , Su haƙura su bar kome zuwa lokacin da za'a haifi abunda yake cikin nata ya girma zuwa munzalin da shi ko ita da kanta zata sadauƙarwa da 'yar uwar ta/shi ɓargon ta . Falmata tayi kuka akan wannan batun , a ganin ta Baban Mama baya tausayin Mama , yaya zai ce har sai Mama ta jira shekaru kusan ishirin nan gaba tana fama da wannan ciwon ? Wannan ya ƙara mata damuwa duk ta rame sai haske da ta ƙara yi da ƙyalli irin na mata masu ɗauke da ƙaramin ciki , Ana gobe tafiyar su bayan sun dawo daga ganin likitan ta , inda ya bata tsawon watanni goma nan gaba da zata sake dawowa a duba idon saboda  sanar da shi batun komawar su gida da suka yi , Sannan babu wata sabuwar matsala da ta taso akan idanun nata sai ma cigaba da ake samu kaɗan-kaɗan ganin nata yana ɗan sake ƙarfi duk da dai har yanzu bata gani tar-tar . Yossouf ya dubi Falmata wacce ta rungume Mama akan cikin ta suka yi lamo akan kujerar ta naɗe musu jiki da babban bargo ɗaya , duk kuwa da cewa sanyi ya ragu sosai ƙasar . "Fatima nace ki daina ɗaura Mama bissa ga cikin ki , kada ta miki ciwo ko kuwa abunda ke cikin ki .' Ɗan murmushi tayi bata ce kome ba illa sake rungume Mama da tayi wacce take taɓa ƙailula saboda rashin jin daɗin jikinta , Ba tare da ya janye idanun sa daga kan su ba ya cigaba da cewa , "dagga mun koma gida zan kai Mama école ko doumin ta huttashe ki , ki yi fama da kan ki kadda ta kawo matsala ga Baby ,  Da sauri ta katse shi , "Baban Mama a yanayin wannan jikin na Mama zaka kai ta makaranta , da dai ka dauka mata mai koyarta darussa a gida , makaranta yara zasu doke ta ko kuwa ta yi tsalle-tsallen da zai iya kawo tashin ciwon ta , ga.... Shima katse ta yayi cikin taushin murya , "Fatima ciwon Mama ai bai hana karatu , baki da labarin masu ɗauke da irin cutar ta har suna kaiwa ga matakin kammala jami'a har ma suyi aikin bautama ƙasa , al'umma kouma ta ci moriyar su ? "Mama zata tai ecole inshaAllah , ki dunga ƙarfafa mata a matsayin ki na ouwa gareta , wataƙila watarana ita ma ta zam likita , Ya ƙarasa zancen zuciyar sa cike sa burin son Allah ya gwada masa wannan ranar , "Allah ya sa Baban Mama , Allah ya raya mana Mama mu kai zuwa ga wannan ranar . Ta amsa fuskar ta ɗauke da murmushin da ta kwana biyu bata yi irin sa ba , *** Washegari bayan sun kammala duk wasu shirin su , sun haɗa kayan su da suke son komawa da su gida a cikin manyan Jakankunan su da suka zo da su alhalin babu kome a cikin su , a yanzu cike suke da tarin suturu , magunguna , zuwa kan kayan buƙatun su na yau da kullum da suke son tafiya da su . Sauran tarkacen da bashi yiwuwa su kwasa Youssouf ya zubda a babbar shara , bayan sun gama tattara kome nasu , Youssouf ya zare katin kuɗin sa da ake cirar kuɗin ruwa da na wuta tare da gas da suke amfani da shi tsawon lokacin , Suka jawo jakankunan su waje , inda suka tarar da waɗanda suka basu hayan gidan suna jiran su , miƙa ƴsn mukullin gidan ya yi , Suka yi musaba tare da godewa juna , ya matsa kusa da Musa da Ramlat wanɗanda suke tsaye , Fuskar su cike da alhinin rabuwa da zasu yi a yau bayan ɗan takaitatcen zaman jin daɗi da mutunta juna gami da shaƙuwar da ta fara shiga tsakanin su , suka gaisa Basu wani jinkirta ba suka shiga mota baki ɗaya da kayan su Musa ya jaa su kai tsaye zuwa Airport inda jirgin da zai sada su da ƙasar su kai tsaye daga nan harabar tashi da sauƙar jiragen sama na birnin New York zuwa harabar tashi da sauƙar jiragen sama na Niamey . *** Ƙarfe huɗu na agogon Niger jirgin su ya dira , inda daman direban sa na musamman yana jiran sa , ba wanda ya ke kai Falmata makaranta da daukota ba wanda shine yake kai Hajja Maiduguri , Wannan direban sa ne musamman daga wajen aikin sa , da daman sun san da isowar sa , Gidan sa ya nufa da shi duk cewa Falmata ta so su zarce asibiti saboda Amai da Mama ta dunga yi tun a cikin jirgi , jikin nata ba daɗi sosai , Har cikin gidan direban sa ya shiga da motar , ya buɗe musu ƙofar motar suka fito , Youssouf ya riƙo hannun Falmata da ita ma ba wani jin daɗin jikinta take ba ɗauriya kawai take yi amma baki ɗaya zuciyarta hautsinawa take dan haka ne ma ta ƙi cin kome , yunwa kuwa sai sasuƙar ta take yi , Ya ɗauki Mama a kafaɗar sa wacce take kukan zafi tana son a cire mata kaya masu ɗan nawin da suke jikinta saboda sauyin yanayi . Kai tsaye suka doshi cikin gidan sojan da ya ɗauko kayan su yana bin su a baya , bakin su duk ɗauke da Sallama suka shiga , shiru babu wanda ya amsa musu domin babu kowa a falon . Da shigar su falon Yossouf ya zaunar da Mama bisa kujera , gefen Falmata ta sanya hannu ta jawo Mama jikinta , Shima zagayawa yayi ya zauna daga ɗaya sashin kusa da ita , Bayan direban ya gama shigo da kayan Youssouf ya yi masa iznin tafiya , Ƙarasa haɗe sararin tsakanin su yayi , tare da riƙo hannun ta da duk ya saki , "Fatima me zaki ci ? Hajja zata dafa miki , ina ga ma bata san mun dawo ba , "Mama ki je ɗakin Hajja kice mun dawo , Duk da cewa ba ƙarfin jiki ta cika ba sai ta miƙe , "to Papa , "Baban Mama bari na ƙira ta da kai na, Riƙo ta yayi ya ɗorata baki ɗaya akan jikinsa , yana jin yadda jikin nata ya ɗau ɗumi , "ki bari Mama ta ƙira ta zata iya , kar ki wahalshe min da kan ki , shafa saman idanun ta yayi da suka ɗan shiga ciki , kin zauna da yunwa Fatima meyasa , Ƙarasa narkewa tayi a jikin sa tana jin daɗin irin riƙon da ya yi mata , "Nagaji da irin abincin su ne , " To me zaki ci Hajja ta dafa miki yanzu  ?   " Ƙuli-ƙuli mai sugar raina yake so , Ɗan zare ido yayi sai kuma ya saki sassauƙar dariyar da har ta isa ga kunnuwan Mama wacce take ta faman tura ƙofar ɗakin Hajja ta gagara buɗewa , Ita ma dariya ta sanya jin sautin dariyar Babanta , tana sake tura ƙofar ta ga an buɗo , a hankali ta ɗaga kai tana kallon farar matar da take tsaye a gaban ta da bata kai ga taɓa ganin fuskar ta ba , Yakaka wacce fitowar ta kenan daga wanka ta ji ana taɓa ƙofar ta zo da saurin ta ta buɗe ga zaton ta Hajja ce wacce ta tafi kasuwa sayo kayan miya tun da ta idar da Salla , Fuskar da ta ci karo da ita a zahiri ta sa zuciyar ta sauya bugu , tamkar a mafarki ta gan ta a gaban ta duk kuwa da cewa tana da masaniyar dawowar su a tsakanin yau zuwa gobe a cewar Hajja ,. Bata san lokacin da tayi durƙuso ba a gaban ta , ta miƙa hannuwanta biyu ta tallafe kumatun ta bayan ta dai-daita tsawon su , "Mama , Ta ƙira sunan ta da wani irin sauti ciki-ciki , rungumeta take nufin yi sai taji yarinyar ta janye jikinta a hankali ta yi baya-baya , Kafin ta juya da ɗan gudun ta tana ƙiran "Papa , Mama , watta ce cikin ɗakin Hajja , Da sauri ta yunƙura ta bi bayanta saboda ji da tayi gaba ɗaya zuciyar ta ta afu ga 'yar ta , wani irin shauƙin so da ƙaunar 'yar ta ke kwaranyowa a zuciyar ta , Da taka kafafunta a falon Falmata ta ɗago kan ta , daga ƙirjin Youssouf , tare da chanjin bugun zuciyar ta , a take ta bijiro mata a cikin rai Yakaka, ta ambata a zuci , Tare suka ƙaraso da Mama da ta tafi da gudu ta hau kan jikin Babanta da Falmata ta ɗaga , Turus tayi , idanunta ya sauƙa akan su  , da wani irin yanayi ta dubi ƙwarar idanun Youssouf da suke cikin nata da yanayin firgici ɓaro-ɓaro a cikin su , Cikin daƙiƙa kaɗan ta janye idanunta daga kansa ta mayar su ga Falmata , wacce take ware idanun ta da suke hango mata dusu-dusun farar mace sol a tsaye , wacece wannan ? Hajja kenan ? Girman da Falmata ta yi tare da gogewar da tayi basu jirkita mata kamannin 'yar ƙanwar ta ba , so take ta taka taje ta rungumeta , sai dai wanda ta hango ta jingine da jikin sa ya mata tarnaƙi . Bata motsa ba daga inda ta ci birki , illa Muryar ta da ya ratso shirun da wajen ya ɗauka ta ƙira sunan ta "Falmata na , Muryar ta ta sauƙa da ƙaƙƙarfan sautin da ya wuce yadda ita ta yi maganar a kunnuwan Falmata , Waigawa tayi sashin da Youssouf yake a daskare , muryarta na rawa tace ' Baban Mama muryar Yayata nake ji ta ƙirani , Muryar Maman Mama , Muryar Yakaka na , yan yién . Yakaka wacce Hawaye ya fara sauƙa daga gurbin idanun ta tace , "Falmata umaa yammana3 , umaa bangie3 , are3 nayie3 Falmata , Falmata are3 nayie3 , are3 Falmata kiramie nyie . Sai ta miƙe a hankali daga gefen sa tana jin wani ƙaƙƙarfan yanayi na kusancin su na ingizata yana cire mata duk wani tsoro da shakku daga ran ta , Yakaka ai wata sashi ce na daga tsokar jikinta babu shakka wannan Yakaka ce tsaye a gabanta , wannan farar inuwar da take gani ba kowa bace illa Yakakar ta  , 'Yar uwar ta , Ashe Yakakar ta na raye , ashe bata mutu ba ? ??? Yakaka bata jira ta ƙaraso inda take ba ta tafi ta rungumeta , zuwa lokacin su dukkanin su biyu kuka suke da sauti , Kukan da kowaccen su ta jima tana neman 'yar uwa da zata taya ta yin sa , kukan kewar junan su , kukan tausayi da ƙaunar junan su , kukan tunowa da farkon fari , mafarin faruwar walagigin su , Mama wacce tayi lamo a jikin Baban ta ɗago kan ta tana kallon fuskar sa , "Papa qui est cette femme étreignant ma mère? qu'est-ce qui les fait pleurer? ( Papa wacece wannan matar da ta rungume Mamana?  Meyasa suke kuka ? ) Tamkar wanda ya farka daga bacci haka ya firgita da tambayoyin Mama , kallon ta yayi kafin ya mayar da ganin sa kan su da suka ƙarasa zama a ƙasa har yanzu suna kuma rungume da junan su tamkar idan ɗaya ta bar ɗaya ɗayar zata gudu ko ta ɓace . Motsa laɓɓan sa yayi da nufin yin magana sai dai ko kalma guda ta gaza fiddo da kan ta , wani irin zullumi mai tafe da tsananin firgici ke samun matsugunni a ƙarƙashin ran sa , "Yakaka bata mutu ba ta dawo ?? Wani  irin sarawa kansa ya yi lokaci guda , take gumi ya shiga tsattsafo masa tunanin makomar auren sa da Falmata yana kassara masa duk wani guntun ƙarfin sa . Assalam Alaikum masu karatu , Da fatan duk kuna lafiya ? Ina miƙa sakon gaisuwata a gareku da fatan alheri a duk inda kuka yi bigire . za ku ce ya ta rage hannu ?? 😜😂  Ban san ko kun fahimci MHR ya fara naɗe kayan sa ba ?  Me zai hana kafin lokaci ya gwada mana ƙarshen MHR dukkanin masoyan MHR na fili da na ɓoye su yunƙuro , kuyi ɗango ku gwada min ƙaunar ku ga MHR ta hanyar bayyana ra'ayoyin ku tare da danna ɗan tauraron nan , da ni kuma na gwada muku irin tawa bajintar ta hanyar ƙure muku ......................ɗan..ɗan...ɗanliti😂🏇 ƙur-ƙet , ah to meye ? Ya wuce na dunga yin update kullum har a gama ?? Ƙurunƙus 🙅🤓 Nagode. [11/23, 7:08 PM] +234 706 503 6187: MAFARI ( Hargitsin Rayuwa ) Umm'muaz 41 Shigowar Hajja ita ta tsagaita kukan Yakaka da Falmata, Da girmama juna suka gaisa ita da Biyamuradi Youssouf wanda ya samu da kyar ya iya harhaɗa kalmomin amsa gaisuwar Hajja , saboda jin sa da yake gaba ɗaya a birkice a gigice, tamkar babban mai laifin da yake jiran hukunci daga Alƙali , da yana da dama da tuntuni ya ɓace ɓat . Hajja ta mayar da ganin ta gare su sai tayi saƙare tana bin su da kallon Al'ajabin yadda suka ƙaƙwume juna suna shiƙar kuka , " ku kuma yaran nan lafiya kuke kuwa ?  Uwarɗakina Falmata ya daga zuwa sai kuka ? Ai ke yanzu kukan ki ya ƙare , farin-ciki ya kamata ki ta tayi  'yar nan , bari kuka Falmata . Falmata ta ɗago kan ta daga jikin Yakaka idanun ta da hawaye amma tana ɗan murmushi tace , " Hajja ke ce wannan ? Bata jira ta amsa mata ba ta ɗora da cigabada cewa , "Dole nayi kuka Hajja , wannan da take gabana yanzu ita ce Yayata da nake baki labarin ta Yakaka Mamar Mama , ta dawo ashe bata mutu ba , kukan murna nake Hajja , duk duniya a yanzu bani da wanda ya wuce ta . Hajja ta ɗan taɓe baki , tana satar kallon Youssouf da yake wuƙi-wuƙi da ido yana shafa kan Mama da take jikin sa tana bin Yakaka da kallo , " aifa na ganta , labari kuma ya iske mini tun muna can , ai tare muka zo , ina gida lokacin da ta dawo daga inda tayi mafakarta tsawon shekaru , " Uwarɗakina lafiya ta samu ko ? , wallahi nayi murna , nayi murna Allah dai ya sakawa Babban soja da dubun Alheri , samun mijin da ya wuce shi a wannan zamanin akwai wuya , ki kama mijin ki ki riƙe ƙam-ƙam , Allah ya barku tare ya baku zuri'a masu yawa da Albarka , Shiru falon ya ɗauka aka rasa mai ƙarfin guiwar Amsawa , Ga Yakaka mummunar addu'a ta danganta addu'ar Hajja da ita dan haka tace " ba amin ba, cikin ranta tabbas ta san da Hajja take wannan kankanbar bata san wanene Youssouf bane ,  A sanyaye Youssouf ya miƙe riƙe da hannun Mama da taƙi barin jikin sa , so yake ya kaucewa sake haɗa ido da Yakaka , yana buƙatar wani ɗan saƙo da zai shiga ya rakaɓe ya haɗa kai da bango ya yi kuka ko zai ji sauƙin tashin hankalin da yake ciki , fili da baɗini bai ji daɗin dawowarta ba , bai ji daɗin bayynuwar ta ba , ya so da ta cigaba da zama a matatciyar ta tulin addu'o'in sa na riskar ta , Taku ɗaya yayi yana ajiye na biyu , yaji sun ƙira sunan sa a kusan tare , "Baban Mama , "Yusuf , Hatta hantar cikin sa sai da ta kaɗa , da jin tashin muryar ta da kaushi a ƙiran sunan sa , A firgice ya waigo idanun sa cikin nata da yake iya hango ƙiyayya da tsana masu ɗinbin yawa , ji yayi kamar ya durƙusa guiwa biyu ya roƙeta kadda ta fasa sirrin dake tsakanin su a yanzu .  Da sauri ya mayar da ganin sa ga Falmata wacce ya ga ta sunkuyar da kan ta yana iya hango bayyanar wani irin yanayi a tare da ita , "Na'am Fatima yace , Falmata wacce ƙiran sunan sa da Yakaka tayi ya ankarar da ita tare da tuno mata da matsayin Youssouf ɗin Na asali ga Yakaka , jikin ta yayi sanyi da tasowar wani yanayi mai suffar tsoro-tsoro daga ƙasan ranta , cikin dabarbarcewa tace , " un daman nace ga Maman Mama fa ? Baku gaisa ba ? Zaka fita da Mama bata gaishe da Maman ta ba , Da sauri ya saki hannun Mama , bai yarda ya dubi fuskar Yakaka ba , yace " sannu dai , Da sassarfa ya ƙarasa barin falon Mama ta ƙara da gudu ta bi bayan sa duk ita zuwan Yakaka ya takurata , Kallon tsanar da Yakaka ta bi Youssouf da shi akan idanun Hajja wacce ta kasa ta tsare tana bin duk wani motsin Yakaka da ido , Moɗe baki tayi kafin ta ce , " ke Yakaka tashi mu shiga daga ciki , ita Falmata ta bi sawun Mijinta tunda dai bata bar shi shi kaɗai ba , wannan zaman naku na ke kuka ita juyayi baya haifar muku da ɗa mai ido ba , " Abunda ya wuce ya riga ya wuce a bar tuna shi ana koke-koke kun ji ko ? Daga Yakaka har Falmata babu wacce ta amsa mata saboda kawo yanzu hankulansu ya dawo jikin su daga ruɗanin murnar da suka shiga na sake ganin juna , Kowacce kuma ƙwaƙwalwarta ta fara aiki cikin gaggawa da fuskantar ƙalubalen dake gabanta , Ga Yakaka yadda zata tunkari Youssouf yaso ruɗata da ta ga ya ƙara girma da haiba , ƙwarjinin sa yana neman tsorata ta sai dai daga ta tuna shi da munanan ɗabi'un sa sai ta ji duk ya koma fanko a idanunta , tafi shiga damuwa akan yadda zata fayyacewa Falmata gaskiyar kome , yadda ta hango nutsuwa a fuskar Falmata ta san zuciyarta zata yi baƙi idan ta san gaskiya wataƙila ma ta tsaneta ita da kan ta da ita kuma bata fatan hakan, ita yaya zata yi ne ?? Falmata kuwa wani irin tsoro ne ya cika zuciyarta tare da zullumi , bayan murnar dawowar Yakaka , zuwa yanzu abunda zai biyo baya takewa Fargaba . na farko tsoron rabuwa da Mama , Allah ya shaida bata fatan rabuwa da Mama ko na yini guda , sai kuma ga Allah ya dawo da Mahaifiyarta , ta san dole Uwar ta buƙaci 'yar ta , Yakaka zata rabata da Mama ne ko zata barta ta cigaba da riƙon Mama ? Tsoro take ji. Tare da zullumin rabuwar su da Baban Mama ,  mutumin da Alkhairin sa ya yawaita ya tunbatsa a gareta , mutumin da tarin Alherun sa da haƙurinsa da ita ya huda tattaurar zuciyar ta tare da kafa soyayyar sa a ciki , Mutumim da ya zama tsani na samuwar ganin haske a idanunta , mutumin da sanadin sa ta samu ilmin boko da na addini dai-dai gwargawdo,  mutumin da ta riga ta mallakawa gangar jikinta ya tarɓeta da so mai tsanani cike da tausayi da tausasawa  , mutumin da ta riga fara gina rayuwar ta da shi ,mutumin da wani ɓangare na jikin sa yake a cikin ta yana rayuwa , Wani irin narkewa ta ji dukkanin lakar jikin ta na yi , Lokacin da ta tuno yiwuwar rabuwar ta da shi , tunda daman rashin Yakaka ya kawo yiwuwar auren su har ta kai su da rayuwar aure tare yanzu kuma da ta dawo , dole ita zata matsa kenan  , zata tafi kenan , za su rabu kenan ina ma ina ma ? Sanyi ta ji ya fara kaɗa ta duk kuwa da cewa a zahiri zafi ake yi , Hannun ta da yake cikin na Yakaka ta dunƙule , jin haka ya dawo da Yakaka daga tunanin da ta nausa a ciki , da sauri ta riƙe hannun Falmatan , "Falmata kun dawo baku ci abinci ba ke da Mama ? Mun yi muku girki fa , kuma ma na kawo miki tsaraba ban san ko Mama ma zata iya ci ba , ƙuli-ƙuli ne mai sugar irin naki kina so  ? "ina so Yakaka kawo mun zanci , na daɗe ban ci ba , kamar kin san yana raina , yanzu na cewa Bab... Sai tayi shiru bata ƙarasa ba , ji tayi tana tsoron ƙiran sunan sa a gaban Yakaka ko me yasa ? Yakaka ta miƙe a hankali , ta nufi ɗakin da suka yi masauƙi , Hajja wacce tayi jugum a zaune tana binsu da kallon tsanaki , tace 'Uwarɗakina kar fa ki sanya kan ki cikin damuwar kome ko domin abunda kike ɗauke da shi a jikin ki damuwarki hatsari ne maigirma , da yardar Allah haƙuri tare da ƙaunar ki ta gaskiya da riƙo da zumuncin da kika yi basa bari ki tozarta ba , ke dai ki cigaba da yin kome domin Allah kin ji ko ? Gyaɗa kai kawai tayi , "nayi muku tuwon shinkafa da miyar kubewa , ga kuma farfesun dantsen sa , akwai dafadukar shinkafa 'yar uwar ki ta mata sarrafawar turawa a ciki wacce zaki ciki ? Ƙarasowar Yakaka ya sa bata amsa ba , hankalinta ya koma kan Yakaka da take tahowa , ƙewar 'yar uwar ta tare da wannan ƙaunar mai tarin yawan suna taya ta binne duk wata damuwar ta tare da ƙarfafa mata , "Yakaka ashe kina da tsawo haka sosai , ga ki kuma fara sol Yakaka mai kyau da ke tubarakallah ,  bani labarin kamannin Maman mu da Baban mu da wa ni nake kama a tsakanin su ? Yakaka wacce take sunce ledar ƙulin ta gama kuncewa ta ɗibo biyu a hannun ta , tana murmushi ta kai ɗayan bakin Falmata da ta ga tahowar hannun Yakaka ta buɗe baki ita kuma ta jefa mata ƙulin , " Da Baa kike kama Falmata sak ma kuwa kawai tsawon sa ne baki samu ba , ni kuma da Maman mu nake kama sak kawai ban kaita haske ba , Ƙurus-ƙurus ku-rus , Yakaka ta taune ƙulin da ta jefa a nata bakin , ta cigaba da cewa " Daman an raba , ni da Bulama kamar mu ɗaya ke kuma da Baana kuma kamar ku ɗaya (sulum fut ) baƙaƙe siɗik , ta ƙarasa zancen da sigar tsokana , Yamutsa fuska Falmata tayi , kafin ta ce , "Amma ai Baa kullum yana cewa fararen mutane basu da ƙarfi da dauriya , mu baƙaƙe mun fi ku , Yakaka kin tuno da karon mu da Biri a gonar Baa ? Wata sassauƙar dariya suka kwashe da ita lokaci guda , Yakaka wacce ta fi Falmata dariya muryar ta cike da amon dariyar da take yi ta ce cewa za kiyi ranar da kika sumar da ni a garin dukan Biri , Wannan karon hatta Hajja da take kallon su sai da ta murmusa , sannan ta ce tayaya ta sumar da ke Yakaka daga dukan Biri ?? Siririyar Muryar Falmata cike da dariya ta fara cewa , "Hajja lokacin girbi ne Baa ya kai mu gonar sa domin muyi masa gadi , muna zaune yin gadi da rana tsaka , sai wani ɗan Biri ya shigo gona , Yakaka ita ta gan shi ta dunga binsa da wata sandar da Baa ya bamu tana son doke shi amma Birin nan sai tsalle-tsalle yake yana gudu yaƙi barin gonar , ƙarshe dai yayi tsalle ya hau kan Yakaka char ya tsaya atsakiyar kan ta , Sai yakaka ta ce "Falmata nace "Na'am ,tace Birin nan yana tsaye akaina ga sandar nan zan wurga miki , inda kike jin muryar ta za ki doke ta sama kaɗan ki buga masa da ƙarfi ɗan iskan Biri ɓarawo , Nace "to Yakaka , ta kuwa wurgo min sanda na ɗauka , "Hajja na faɗa miki da na ɗaga sanda kin san dai ba gani nake yi ba a lokacin, na ɗaga ta da ƙarfin gaske , lokacin da. naji Yakaka tana cewa kai-kai-kai amma na riga na wulwula sanda sai kawai na rafka a zatona alama take min na inda zan bugawa sandar watau a kanta , Ɗif na ji Yakaka tayi shiru , "Hajja ashe Yakaka na rafkawa sandar Biri kuwa tuni yayi tsallen sa , Yakaka kuma ta some , Ta ƙarasa bada labarin tana sakin shisshiƙar dariya tare da kwanciya bisa kujerar da take kai , ba Yakaka ba hatta Hajja , dariya take yi sosai , Yossouf da yake tsaye ta bakin ƙofar falon saboda hankalin sa da ya kasa kwanciya a zaman sa a falon sa , cikin duk daƙiƙa guda zato yake yi Yakaka zata sanar da Falmata kome , Da shi kuma ko kusa a yanzu bai shiryawa tarɓar tashin hankalin da zai iya biyo bayan hakan ba . Baya yayi yana dariya da haƙoran sa kwarai labarin wannan ƙatoɓarar da Falmata ta yi ya bashi dariya , Yana shiga Falonsa wayar sa da take ajiye akan kujera ta sake ɗaukar kiɗa sunan Tafeeda ne ke yawo akan fuskar wayar , Ji yayi damuwowin sa sun sake yi masa rubdugu , zama yayi daga kan kujera ya ɗau wayar ya riƙe , ya akayi ma Tafeeda yasan dawowar sa, ?  duk ƴan mintoci kenan da sanya layin sa na nan a waya , Shi a yanzu baya buƙatar ƙarin wasu damuwowi , yasan Tafeeda ƙudirinsa shine ya raba shi da Falmata da shi kuma ba shiryawa hakan yayi ba , ba kma ya jin zai taɓa shiryawa har abada, Danna wayar yayi ya sa a silent saboda Mama da ta samu bacci kar ƙaran waya ya tadda , tagumi ya rafka da hannunsa biyu yana jin yadda cikin sa ke ƙugin yunwa amma ba damar cin abinci , Bayan sun tsagaita daga dariya , Hajja ta kallesu tana nazarin tarin ingantatciyar ƙaunar da ke ga junan su , a hangen ta irin na manya ta fuskanci kowaccen su tana ƙokarin binne damuwar ta ne daga 'yar uwarta saboda zallar ƙaunar da suke yiwa juna , idan kuwa hakane Madallah da irin wannan ƙauna ta tsakani da Allah , Miƙewa tayi tare da cewa , "Yakaka yayar Falmata zo muje daga ciki ki ga irin 'Ya'yan itatuwan su na nan Niger ba irin namu na Nigeria ba , "Uwarɗakina Falmata a kaiwa Mama abincin kadda yunwa tayi mata lahani  , tana sashin Baban ta ai kin san hanyar ko ? Kin kuma san kitchen ɗin ga shi nan , "nasan Hanya Hajja , Falmata ta furta hakan tana jin son ta tafi ga Mijinta ta ga halin da yake ciki , sannan ta fuskance shi ko zata iya ganin wani sauyi a tare da shi na daga zallar ƙaunar da yake nuna mata muddin suna tare , a sanadin bayyanar Yakaka ? Yakaka bata ce ƙala ba ta bi bayan Hajja , har ta ɗan gifta Falmata , sai ta ji ta ƙira sunan ta , "Yakaka nyei Juyowa tayi fuskarta da Murmushi "Na'am Falmatan nyei "Yanzu zan zo da Mama tayi miki hira duk da bata da lafiya sosai , amma ta iya hira sosai , zan kawo miki ita . Murmushi kawai Yakaka tayi ta juya tana ƙarasa barin wajen , Suna shiga ɗakin ta cewa Hajja , "Hajja ina 'ya'yan itatuwan ? Mu ga irin su ? Kallon tsakar ido Hajja ta yi mata , "Yo ina kuwa wasu 'ya'yan itatuwa nan ? Kin tsare yarinya kin hana ta kaiwa mijinta tattattun 'ya'yan itatuwa tayi aikin lada ubangiji ya samar mata da lambun 'ya'yan itatuwa a Aljanna , ke haka ake yi yanzu tsakani da Allah ? Haba Babba uwar Mama . Kallon Mamaki Yakaka tayi mata , ta samu waje ta zauna daga gefen gadon dake ɗakin "kenan Hajja dai ba gaskiya kika faɗa min ba wayo kika min dai ko ? Hajja bata dube ta ba ta fara ninke gyalen ta , ta bata amsa da " to kuma dai , karo ɗaya ai ko da ƙwai da dutse a yi sa . Shiru Yakaka tayi bata ce kome ba , cikin ranta damuwarta ce ta dawo sabuwa fil akwai wani alamu da ta hango tare da Falmata wanda bata fatan tabbatuwar sa , Falmata bayan ta jera abincin su da ta tarar a rurrufe cikin mazubi , sai ta ɗauka ta nufi sashin Youssouf da ta san yana ta harabar gidan duk kuwa da cewar bata taɓa zuwa ba , sannu-sannu take tafiya saboda duhun dare da ya fara shigowa daf ake da ƙiran sallar Magariba ,  tare da taimakon hasken fititulun da suke girke a harabar gidan da suka kunna kan su , ta iso Bakin babar ƙofar ta tsaya tayi sallama , daga ciki Youssouf wanda tuntuni yake kai kawo a cikin falon ya taho da saurin sa jin muryar ta ya buɗe mata ƙofar Tunda ta shigo falon Biyamuradi yake binta da kallo mai wuyar fassara , so yake ya tantance yanayin da take ciki , amma ya gaza gano wata alama, maimakon haka sai ya shagaltu wajen kallon tsarin kyakkyawan jikin ta da take sanye da doguwar rigar roba da ta bi jikin ta lafe , koyaya ta motsa sai wani sashi na jikinta ya ɗau hankalinsa . gefe guda Mamakin kansa yake yi yadda yarinya karama take mamaye tunaninsa a duk lokacin da suke tare ko ya koma gida. Akwai wani abu game da Fatima Zahra da ya kasa fasaltawa a ransa da a farko yake yawan sakawa a ransa cewa saboda irin kulawar da take yiwa 'yarsa ne. Sai dai zuwa yanzu ya hiƙaƙancewa kansa cewa ƙaunar Fatima ɗarsuwa tayi a cikin ransa tun a ranar da ya soma ganinta , alhalin lokacin bai san cewa ma zata zam mariƙiyar ɗiyar sa ba . Akan ɗan teburin dake tsakiyar falon ta ajiye farantin hannunta wurin da yake zaune ta waiga , cikin kwantatciyar murya tace "ga abinci". Shiru taji kamar babu kowa waigawa tayi sai dai duhun da yake falon tare da rashin ƙarfin ganin ta sun hana ta damar hango shi , wanda yana sane ya rinka tafiya a hankali , Ji tayi kamar abu na nenam rufeta ta baya ta dan ja jikinta kadan sai kawai taji tayi karo da mutum. Gabanta ne yayi wata irin faduwa ta rikice tana neman hanyar barin wurin saboda tsintar kanta kawai tayi da kasa sakewa da shi yadda suka saba ,  shi kuma yaki matsawa sai ma hannuwa da ya saka ya zagaye kunkumin ta tare da haɗa bayanta sosai da ƙirjinsa "Hankali Zahra" yace da wata irin murya a daidai kunnenta har tana jin saukar numfashinsa. "Uhmmm zan wuce ka matsa" ta hado kalaman ta furta a hankali. "Baki zuba min abincin ba zaki tafi?" Ya ce yana karewa kyakkyawar fuskarta kallo, bayan ya juyo da ita ya kamata suka zauna , Turo baki tayi tana jin kanta a takure  "ni da kasan bana gani sosai idan dare yayi ?" kuma ai kasan ban iya zuba abinci ba . Ya dage gira daya "yau kuma? Na dauka Zahra ta iya komai ashe da sauranta tunda bata iya zubawa miji abinci ba." Ya sake matsawa kusa da ita daga zaunen da suke , Sai dai bai bari jikinsu ya hadu ba saboda ko kadan bai yarda zai iya mallakar kansa ba a yadda yake ji ba , saboda shi da kansa buƙatar inda zai sanya kansa a rarrashe shi yake , da kuma ya tabbata Fatiman tasa a wannan gaɓar bata isa bashi kulawar da yake so ba ,  "gashi yau da hannunki nake so ki bani" Yace mata yana murza ƴan yatsunta da ya riƙe cikin hannunsa Yana kallon yadda idanunta suka kara girma kirjinta yana hawa da sauka cikin sauri da firgicin da bai san dalilin samuwar sa ba a dai-dai lokacin , "me zan baka?" Tace muryar ta na ɗan rawa , "Abinci mana yadda kike bawa Mama" Bata san lokacin da tace "kai alanguro Yarima" cikin wani irin amon murya mai nuni da tsoro da mamaki ba. Murmushi yayi , tare da kai hannunta bakin sa ya sumbata ,   "me kika ce ? Aina kika ji wannan sunan ? Sake ƙira muji kamar naji kince wata kalma ta daban me kalmar ke nufi ?   Shiru tayi tana murmushi , "to shikenan idan baza ki zuba min ba  , bakya ƙara fita a ɗakin nan sai gobe , Bai rufe baki ba ta laluba ta ɗau farantin , Tana turo baki ta zuba abincin tana faman kunkuni "yaushe kaji nace ba zan baka ba to?" "Afuwan nayi tunanin kin fada a zuciyarki ne" ta dauki cokali ta ciko shi taf "bude" tace kamar tana magana da baby. Cokalin ya kalla a tsorace "duk wannan a bakina Fatima?" Tayi murmushin keta "ba irin na Mama kake so ba? Haka nake bata" "Amma ni da hannu nake so" Tunanin yadda za ta tsere takeyi ta ajiye ta diba da hannunta tayi sama dashi tana laluben bakinsa,Hannu taji irin na mazan da suke gwagwarmayar yau da gobe ya rike tsintsiyar hannunta a hankali ya kai bakinsa ya ci kadan sai da ya hadiye ya kara sai a karo na uku taji yatsunta gabadaya cikin bakinsa. Ita kanta bata san yanayin da ta tsinci kanta ba bare kuma shi uban gayyar da yake jin inama bakin tsiwar ya samu haka ba yatsunta ba kawai, "Ashh Alangubro zaka cinye min yatsu ne ? " da zan iya haɗiye ki ma baki ɗaya da na haɗiye ki Fatima , da kuma hakan shine kaɗai zai fiddani daga zullumi Bata ce kome ba sai murmushi kaɗan da tayi , cikin ran ta tana aiyana , "ina ma da zata iya shigewa cikin jikinsa ta fake wataƙila da rabuwar su baza ta kasance ba , Cigaba tayi da ciyar da shi abincin , kafin ta ji ya riƙe hannun ta , "na ƙoshi Fatima , buɗe bakin ki na baku ke da Baby , Bata musa ba ta buɗe baki ya shiga ciyar da ita , ita ma kaɗan ta ci tace ta ƙoshi , "kaɗan kika ci Fatima , ki ƙara saboda Baby ,, "Na ƙoshi , ai kaima kaɗan ka ci , Bai ce kome ba , sai jawo ta da yayi jikinsa ya haɗe ta da ƙirjinsa tsam-tsam , Cikin kunnen ta yace " ina sonki Fatima Zahra , Lumshe idanun ta tayi , wasu siraran hawayen da bata san dalilin sauƙar su takamaimai ba suka silmiyo suka sauƙa a fatar ƙirjinsa , runtse ido yayi yana jin tausayin ta mai tarin yawa yana mamayarsa a wajen sa babu abar tausayi sama da ita , Sun ɗan yi mintoci kaɗan a haka kafin ya zare ta daga jikin sa , "Fatima , magarib tayi muyi Sallah , **** Bayan sun idar da Sallah sun yi addu'o'i shiru ne ya ratsa tsakani kafin Falmata tace " ina so na shiga wajen Yakaka , Shiru Youssouf ya yi bai ce ƙala ba , saboda har ga Allah bai son su dunga kaɗaicewa saboda bai san da wacce manufa Yakaka take tafe ba , sai dai koma menene yana fatan kar Allah ya bata damar fayyacewa Fatima kome . Jin yayi shiru ya sa Falmata sake cewa "zance wajen Yakaka muyi hira kaɗan , ga shi Mama ma tana ta bacci ba abun na tayar da ita ba ta je Maman ta ta gan ta , "ki rabu da ita , mu je na raki ki kiyi mousu sallama ki dawo nan ki kwanta ki huta , gobe kun yi hira , Youssouf yace haka yana kama hannun Falmata cikin zuciyar sa dan babu yadda zai yi ne , da ba zai bari ta fita ba , Tare suka shiga har falon , basa nan dan haka Falmata ta ƙarasa ƙofar ɗakin Hajja , shi kuma ya dakata daga tsakiyar Falon , Ƙwanƙwasa ƙofar tayi , "Yakaka , na dawo . Zuruf Hajja ta miƙe daga kishingiɗar da tayi tana jaan chasbaha , ta buɗo kofar tare da leƙowa , "uwarɗakina ai Yayar ki tayi bacci tuni , ki koma kiyi kwanciyar ki ki huta kun haɗu gobe da safe ko kuwa , Murmushi tayi , "kai Yakaka har tayi bacci ikon Allah , Ɗan jim tayi sai kuma ta sake cewa ," Hajja to ko cikin dare idan ta farka ki faɗa mata na zo muyi hira tana bacci , ai ta ci abinci ko ? "ta ci abinci sosai ta cika cikinta dam , "to Hajja sai da safe , " yauwa uwarɗakina maza a je ayi bauta a huta , Har ta juya sai kuma ta sake dawowa , "amma , un, un Hajja nace da dai kin taso ta ta koma ɗakina , ina da filo mai laushi irin wanda take so , Yakaka bata son filo mai tauri irin naki Hajja , Wani kallon yatsu-tsu Hajja tayi mata , "aifa Lalle , ita Yakaka jaririya ce kenan ?  To ai wannan surutun da kike ba kai ba ƙafafu ya isa ya tayar miki da ita daga baccin da na lallaɓata da kyar take yin sa , ni wuce Dan Allah ki tafi Allah ya tashe mu lafiya , Ƴar dariya Falmata tayi jin yadda Hajja take yi mata shaguɓe akan Yakaka , juyawa tayi ta kama hanya cikin ranta ba haka ta so ba , so tayi su raba dare suna hira da Yakaka , bata so Yakaka ta ga kamar ta kyale ta ta maƙalewa mijin da bata da tabbacin cigaban zaman su , Youssouf da sauri ya taryeta a cikin ransa yana hamdala da rashin ganawar su , Hajja tana komawa ɗaki ta dubi Yakaka da take zaune akan sallaya riƙe da Alkur'ani tana karatun ta hankali kwance , duk zantukan Falmata a kunnen ta , tausayi gami da ƙaunar 'yar uwar ta suna bin jinin jikinta da gudu , Hajja ta mokaɗe baki , lokacin da take komawa ta zauna a wajen da ta tashi , "ai a wani ƙaulin irin wannan ƙaryar tana iya zama makaruhi , ko kuwa ba haka ba Babba uwar Mama ? Yakaka bata kulata ba ta cigaba da karatun ta , can ƙasan ranta diramar Hajja ta fara bata dariya ,  ** Youssouf , Yakaka , da Falmata kusan kowannen su raba dare yayi bai yi bacci ba musamman Youssouf da ƙiran sallan farko na ƙarfe uku da rabi a kunnuwan sa a hankali ya zame Falmata daga jikinsa wacce itama bata jima da samun bacci ba , ya miƙe tare da shiga banɗaki ya ɗora Alwala , jallabiya ya zira yazo ya tada sallah Nafila yayi tayi har zuwa lokacin da masallatan unguwar suka sa Assalatu , sai ya sallame ya miƙe ya ɗau turare ya fesa tare da ɗaura agogon sa , Fita yayi ya nufi masallaci , bayan ya ja ƙofofin gidan gabaɗaya , Yana bada baya , mutumin da yake maƙale da jikin katangar , ya siɗaɗa kansa tsaye ya shiga gidan , Yakaka wacce ta shiga banɗaki domin ɗaura Alwala sallah ta ga inuwar mutum ya gifta , Tsam tayi tana tunanin waye ? Haka kawai ta ji zuciyarta ta tsinke , sai ta juya da sauri ta fito , sannu-sannu take tafiya , hasken lantarki ya game ko'ina , gabaɗaya unguwar ƙiran sallah ne ta ko'ina , Mutum ta gani a tsaye ya bada baya yana nufar ƙofar falon Youssouf , "Waye ne ta ce Idanunta ƙyar akansa , Chak aka tsaya ba tare da an jiyo ba , Matsawa tayi ta sake cewa waye ne nace ? Ba'a amsa ba , Taku ta fara yi tana kusantar sa , ta zo kusa da shi bata ankara ba ta ji an kifa mata marin da ya gigitata , Tayi taga-taga tana jin wani tsuu a kunnuwanta saboda ƙarfin marin , ta ji takun gudunsa sai dai ta kasa watsakewa daga zafin marin da yayi mata dan haka bata yi wani yunƙuri ba , Lokacin da ta watsake babu kowa a wajen ,lokacin an idar da sallah gari har ya ɗan yi shaa , Yawatawa ta fara yi a wajen tana raba ido ko Allah zai sa ta ga azzalumin da ya mare ta haka ? Ƙarar buɗe ƙofar gidan ya sa ta juyowa a tsorace , wanda ta hango ya shigo ya sa zuciyarta bugun uku-uku , Da sauri ta gyara zaman hijabinta , ta fara tattaro duk wata dauriya da ƙarfin halin da take da shi ta kuma shiga harhaɗa manyan kalmomi masu kaushi da take son yin amfani da su domin su taya ta tunkarar sa , Tirus , Youssouf yayi yana hangota , sarai ya gane ta , wani ɗan guntun yawu ya haɗiye lokacin da tunaninsa ya gama ba shi dalilin tsayuwar ta anan , Gyagijewa yayi a matsayin sa na soja bai kamata ya tsorata har haka ba . Kai tsaye ya nufi ƙofar falonsa yana yin kamar ma bai san tana wajen ba , bai ƙarasa ba ya ji tashin muryarta ta ƙira cikakken sunan sa , " Youssouf Abdul-Aziz Baskore , Sai ya juyo a hankali ya fuskantota da takunsa mai girma , fuskar sa babu alamun ɗaukar wargi , "Gani Yace da ita muryar sa a kwance tamkar fuskar sa ba a murtuke take ba , Cikin zallar ɓacin ran da yake tunkuɗo kansa daga ƙasan ranta da ta wanzu tana ɗauke da shi tsawon shekaru , ta ƙaraso daf da shi da taimakon hasken Alfijir da ya ƙeto ya dusashe hasken lantarkin wajen suke iya kallon fuskokin juna , " Nasan baka san wannan ranar zata zo ba , baka san cewa zan dawo ba , shiyasa har ka samu damar kutsawa cikin rayuwar ƙanwata,  ka cuceni ka yaudareni , ka ɓata min rayuwa , ka lalatamin Asalin 'yata , ka sa rayuwata ta shiga garari  kuma ka zo kana sake cutar min da ƙanwata , a karo na biyu kana sake gurɓata mata rayuwa , Allah zai saka mana abunda kayi mana , kai wanne irin marar imani ne macuci Azzalumi , Mayaudari kuma fasiƙi mazin .... " KI MIN SHIRU . Baisan lokacin da ya daka mata tsawa ba saboda kalamanta da yaji suna tayar masa da hankali , take jijiyoyin kansa suka fito ruɗu-ruɗu , idanunsa suka sauya launi , jikinsa har tsuma yake yi , irin tashin hankalin da yake ji , da akwai bindiga a hannunsa zai iya kai harbi . Tsawar da yayi ita ta farkar da Falmata wacce taji tashin muryar sa a tsawace , shafa ɓangaren da yake tayi ta ji baya nan , Sassauta murya Youssouf yayi yana kallon Yakaka da take masa kallon sheƙeƙe kallon tsana kallon baka isa ba , , zata yi magana ya sake katse ta , "Nace kiyi shiru , zuciyar sa ya ji tana kai kawo wajen tuno masa da girman kuskuren sa , girman laifin da ya yiwa Yakaka , sai ya shiga ƙoƙarin sassauta fushin sa tabbas kome Yakaka zata faɗa masa ya cancanta  , shi ɗin ai ya cutar da its dayawa kamar yadda tace , "ki yiwa Allah kiyi haƙuri , kiyi shiru mu bar kome a tsakanin mu ko dan saboda Albarkacin Fatima da Mama , ki faɗa min duk abunda kike buƙatar nayi miki zan yi , Ya furta hakan muryar sa a ƙasa yana satar kallon ƙofar falonsa, Cikin rashin sanin sa Falmatan tana tsaye daga jikin ƙofar ta bayan labule kalmomin sa na ƙarshe kuma sun cigaba da sauƙa a kunnuwanta tarwai . "Abunda nake so shine kawai ka sakar min ƙanwata , ka sake ta Youssouf ka kuma bani 'yata , Falmata baza ta taɓa cigaba da zama matarka ba muddin ina raye , ka auri Falmata Alhlin babu sanina ba kuma tare da amincewar wani nata ba , ya zama dole ka saki Falmata , ka sake ta nace . Ganin yadda ta birkice masa tana ɗaga sauti tamkar bata cikin hayyacin ta yasa Youssouf ruɗewa yana gudun kar Falmata ko Hajja ɗayar su ta ji maganar , dan haka cikin yanayi na lallaɓa yace , " to naji naji , zan SAKE TA , Wani irin kallon kar ka raina ni Yakaka tayi masa , " yanzu nake son ka sake ta anan idan kuma ba haka ba wallahi zan je masarautar maraɗi a yau ba gobe ba , Da tashin hankali Youssouf yake kallon Yakaka , wacce ta tsattsare sa da ido babu alamun shakku a tare da ita , Gani yayi gabaɗaya ta rikiɗe masa tamkar ba yarinyar nan da ya rainawa wayo , ya kuma yi wasa da rayuwar ta a shekarun baya ba , Falmata wacce hawaye suka riga suka wanke mata fuska kamar ruwan fanfo, ta sanya tafukanta duk biyu ta rufe bakinta ta hana sautin kukan da take yi fitowa , a hankali ta silale ƙasa ta durƙusa tana jin yadda marar ta ta wani irin curewa guri guda .. Assalamu Alaikum masu karatu da fatan kun wuni lafiya ?😍❤ Wai-wai , kai-kakai , yau wacce rana ?? 🤓😂 Uhmmm ai idan har baku daina sakar min bama-baman Comments da likes din ku irin na jiyan nan ba ( ko ma fiye da haka )  Nima kuwa ba zan yi k ƙasa guiwa ba wajen cigaba da sasukar rubutu ba,  "Ah to meye? Ai tuwon girma miyar sa nama,  sannan kuma yaba kyauta tukuici. ❤😍 Amma kuyi hakuri da yadda bana samun damar maida muku da martanin sharhin ku,  idan nace zan dunga daukar waya ba zan kammala aiyuka na da wuri har na samu damar typing ba , duk da haka nayi alkawarin zan bibiyi comments din ku baki daya na bada amsa inshaallah . Nagode. Na manta ko da wacce take buƙatar hayar ɗan Biri saboda tsaro ?! 🐒😂[11/26/2019, 3:24 PM] +234 706 503 6187: MAFARI ( Hargitsin Rayuwa) Umm'muaz 42 Wani ɗan kuka ciki-ciki da Mama ta fara daga can cikin ɗakin kwanan su mai haɗe da nishi shi ya sa Falmata miƙewa daga inda ta durƙushe tana rishin kuka , A duƙe ta ƙarasa ɗakin saboda mararta da take ji ta riƙe , da taimakon hasken lantarki ta hango Mama a ƙasa ta faɗo daga kan ɗan gadon ta da yake dakin , Da sauri ta ƙarasa ta ɗagota tare da rungume ta a jikinta, tana tattaɓa jikin da ta ji yayi zafi rau , muryar ta na karkawa tace , " Mama meyasa kika faɗo daga gado ? Ina ne yake yi miki ciwo faɗa min , ? Kai ne ko ƙafar ki ko hannu ? Ko Bayan ki ne ?? Mama wacce take wani irin nishi ta riƙe hannun Falmata tare da ɗorawa akan cikinta ,ƴar muryar ta da kyar take fita tace , "ciki na ne ,Mama cikina yana ciwo sosai , ki bani magani zan sha ,ina so nayi bacci Mama , Wasu sabbin hawayen ne suka silmiyo daga gurbin idanun Falmata , "sannu Mama ,sannu kin ji zan baki magani yanzu , Bata amsa ba sai nishi da ta cigaba da yi , a hankali Falmata ta dafa cikin nata ta ji yadda ya kumbura yayi ƙem-ƙem ko numfashi da kyar take fitarwa, wani irin tausayi ne ya kamata tare da tashin hankali a lokaci guda ta nemi ciwon marar da take ji ta rasa , Tana dafe da cikin Mama ta fara yin addu'ar samun lafawar ciwo kowanne iri ne , Tashin hankalin da zuciyar ta ke ciki a lokacin yana neman kayar da ita , saboda rikicewa da jikin Mama yake neman yi da ƙarin ƙarfin nishinta ta fara ƙiran Baban ta , "Papa , Papa , Youssouf wanda shigowar sa kenan falon jikin sa a sanyaye ya zauna a kan kujera zuciyar sa cike da tashin hankali kan iƙirarin Yakaka na ya saki Falmata ko kuwa ta je ga iyayensa  , sam bai yi zaton abubuwa zasu rinchaɓe masa ya irin haka ba , Yasan cewa shi mai lefi ne a wajenta amma ko meyasa baza ta saurara su bi kome a sannu ba ? Ƙiran sunan sa da Mama take yi ya sa ya miƙe ya nufi ɗakin zuciyar sa ɗauke da sabon zullumi kan tashin ciwon ta , A kiɗime ya ƙarasa kan su ya tsugunna ta bayan Falmata yana zagaye su duk biyun da hannuwansa da ya kai ya ɗora a cikin Mama inda ya ga Falmata ta riƙe , " Meye ya same ta ? Ciwon ciki take yi , "Papa , Mama ta ƙira sunan sa tana ƙokarin buɗe ido , " na'am princesse ina yake miki ciwo ? 'papa ciki na ka bani magani ina so na kwanta , "Mama ai a kwance kike , bari na kawo magani kisha kafin mu tafi hospitalisé,  "Fatima yaushe Mama ta fara ciwon ciki ? Ya tambaye ta yana kallon fuskarta , Sunkui da kai tayi tana kaucewa ganin Fuskar sa , muryar ta a ɗan dishe tace "Yanzu ne , Bayan ya kawo maganin ciwon ciki ya bata ta sha , ya janyeta daga jikin Falmata ya ɗora ta akan gado , " Fatima kin yi sallah kou ? Girgiza kai tayi tana miƙewa , 'kiyi sallah mu tai da Mama hospitalisé , Bata amsa ba ta ɗau hijabinta ta zura tana barin ɗakin da take jin sa a ƙuntace tunda shigowar sa , Ta kama hanyar da zata sada ta da ciki sashinta , sannu-sannu take tafiya tamkar wacce aka zarewa laka , damuwa yayi mata yawa bata taɓa zaton zuwan wannan ranar ba , saki a tsakaninta da Baban Mama ? Da kowanne daƙiƙa guda tunawa take da kalaman Yakaka , da Baban Mama taƙi yarda wani sashin zuciyar ta da yake bijiro mata da rashin kyautawar Yakaka tare da son kai da take ganin ta nuna ƙuru-ƙuru ya rinjayeta , Ƙoƙari take ta haɗiye tashin hankalinta ta haƙurƙurtar da ranta ta kuma ƙarbi duk wani hukuncin da su biyun da a yau duniya bata da kamar su zasu kai ga yankewa akanta , So take ta rufe ta binne duk wani sirrin dake zuciyar ta a can ƙasan ranta . Sai dai zuciyarta rawa take tana tantamar anya zata iya ?? Hannu ta sa ta tura ƙofar falonta ta shiga , tamkar baƙuwa haka take sanɗa a falon , aiyanawa take nan da ɗan wani lokaci kaɗan kome na gidan zai tashi daga matsayin mallakinta , to ya koma na wa ?? Taƙi yadda ta hasaso ƙarshen lamarin saboda bata jin zuciyar ta zata iya jurar yadda ƙarshen kome zai zama bata son tuno da makomar Rayuwarta . Har ta nufi ɗaƙin ta sai kuma ta dawo da baya ta yi ɗakin da Yakaka take ta ɗan ƙwanƙwasa ƙofar , Yakaka wacce take zaune akan sallayar da ta idar da sallah tana lazumi ta tashi ta buɗe mata ƙofar , " Falmata kin tashi ?   "un bari nayi sallah , ta amsa mata tana ratsawa ta gefenta ta wuce banɗaki , Bayan ta idar da sallah ta ɗaga hannuwanta duk biyu tana addu'a , Ta kwashe fiye da mintoci sha biyar tana addu'o'i , har zuwa lokacin da zuciyar ta tayi rauni gaba ɗaya hawaye ya taho mata , sai ta fashe da kuka mai sauti , Yakaka wacce take azkar ta tsahirta , a hankali ta ɗago kai tana kallon ta , sai ta tashi daga inda take ta dawo kusa da ita , Dafata tayi fuskar ta na bayyana damuwa tace mata   'Falmata meyasa kike kuka ? Wani abu aka yi miki ? Ko baki da lafiya ne ?  Ki daina kuka Falmata ki faɗa min abunda ke damun ki kin ji ? Idanunta suna zubar hawaye ta riƙe hannun Yakaka , muryarta ɗauke da sautin kuka tace , " Mama bata da lafiya Yakaka , Tunda ta tashi tana da ciwo har turai mun je saboda lafiyar Mama amma ba'a dace ba , yanzu ma bata da lafiya zamu tafi da ita asibiti , ki mata addu'a Yakaka . Wani irin tashin Hankali Yakaka ta shiga , zuciyarta na tsananta bugu tace , "Mama tana da ciwo tunda na haifeta ? Aina ciwon yake ? " a cikin jinin ta , idan ciwon ya tashi tana shan wahala sosai Mama abun tausayi ce , Shiru Yakaka tayi cike da tausayin ɗiyar ta , A hankali tace" kije ki shirya ku tafi Falmata , Allah ya bata lafiya , Allah ya warkar da ita babu ciwon da bashi da Magani  , Miƙewa Falmata tayi ta fita zuwa ɗakinta , tana fita kukan ta ya sake dawowa sabo , can cikin ranta neman hanya take da zasu yi magana da Yakaka , so take ta tambayeta meyasa ta ji suna hayaniya da Baban Mama ? Ba tare da ta nuna mata ta san zancen da suka tattauna ba , a sanin ta Yakaka kaifi ɗaya ce wataƙila ta fayyace mata dalilinta , Sai dai rashin samun ƙafar maganar da Yakaka ya sa tayi shiru da tarin damuwarta da ciwon Mama ya zo ya ninka mata , Bayan fitar ta kukan da Yakaka take dannewa ya taho mata, nadama marar iyaka ta sake rufe ta , "Ashe Mama ba ma mai lafiya bace amma ta tsallake ta tafi ta barta ? Haka ta dunga rayuwa da ciwo tun tana jaririyar ta ? Babu tausayi da kulawarta a matsayinta na uwa a gareta ? Ita kuwa anya Mama zata yafe mata idan ta girma labari ya iske mata ? Alƙawartawa kanta take yi tana sake jaddadawa bazata sake yin nesa da ɗiyar ta ba kome runtsi . Kasa zama a ɗakin tayi ta fito falon da babu kowa sai kwarafniyar Hajja daga cikin kitchen , Zama tayi akan kujera tayi jugum cikin allhini , A sukwane ya turo ƙofar ya shigo yana saɓe da Mama wacce tayi luruf , bai lura da Yakaka ba , ya ɗaga sauti dake bayyana tashin hankalin sa , "Fatima ki fito mu tai asibiti jikin Mama ya matsanta kada ta shiga hatsari , Miƙewa tsaye Yakaka tayi tashin hankali bayyane bisa fuskarta , jikinta har rawa yake , Yi tayi kamar zata taka taje inda suke sai kuma ta jaa ta tsaya , idanunta baki ɗaya akan Mama , ba ko dubi fuskar Youssouf ba , Muryar sa ya sa Hajja fitowa da take kitchen tana aiki , turus tayi tana raba ganinta tsakanin Yakaka da Youssouf , "Babban soja barka da asuba , "Barka Hajja yaya hidima ? Mama batta lafiya yanzou zamou tai da itta asibiti , Take fuskar Hajja ta sauya daga mamakin da take yi zuwa Alhini , "Allah sarki kai wannan yarinya kina shan wahala , sannu Mama Allah ya baki lafiya , Babban soja Allah shi baku ladan jinya da hidima da ita , "Amin Hajja ,Amin Ya furta dai-dai fitowar Falmata cikin hanzari  , idanunta hawaye shar-shar suna zuba , da kyar take ganin gabanta , "Hajja ina kwana , tace cikin muryar kuka , Cike da tausayawa Hajja ta amsa , "Sannun Falmata bari kuka haka nan , Allah dai ya bawa Mama lafiya kin ji ? Ai ke kece uwar Mama duniya da lahira . Tana ƙarasowa Youssouf ya riƙe hannunta suka kama hanyar barin Falon , Sai dai taku biyu suka yi , Falmata ta waiga ga Yakaka wacce take tsaye idanunta cike da ƙwallar son sanin halin da Mama take ciki , Inda take hango alamar Yakaka ta nufa , tana zuwa ta lalubo hannun ta , " zo muje asibitin tare Mamar Mama , Babu musu Yakaka ta biyo ta , ganin haka ya sa Youssouf nufar waje bai ce ƙala ba , " Hajja mun tafi , Yakaka tace , bata amsa ba har suka ƙarasa barin falon tana bin Yakaka da kallon mamaki , nisawa tayi bayan wucewar su ,     "o ni Hauwa'u naga abunda yafi ƙarfina , ji bi dan Allah yadda ta bi su ƙobare-ƙobare babu ko 'yar kara ? Geme-geme da ita ta shiga tsakanin su ,   Da ta san tana son ƴar tayi tafiyarta dandi ta bar ta ?? Tawa ta sameni nikam sai nayi da gaske zan hana yin ɓatatciya a gidan nan , *** Dukkanin su biyu a baya suka zauna , yayin da suka shimfiɗar da Mama a tsakanin su , kanta yana a ƙirjin Falmata ta rungume ta , ƙafafuwanta kuma suna kan cinyar Yakaka , Youssouf shi ke jaan motar , Hawayen su duka biyun yana ɗiga akan Mama wacce zuwa lokacin bata a haiyyacin ta , kowaccen su tana tofa mata addu'o'in da ya sawwaƙa gareta , Da gaugawa Likitocin bada taimakon gaugawa na yara suka amshi Mama wacce ta riga ta suma a lokacin , suka rufu akanta suna ƙoƙarin ceto ranta , Bayan kuka da addu'a babu abunda Yakaka da Falmata suke yi , Youssouf kuwa ya kasa tsaye ya kasa zaune , idanunsa sun kaɗa sun yi jaa , bakinsa ya bushe ƙemas , sai kai kawo yake yi yana addu'a Allah ya dawo da lafiyar Mama , Suna nan cikin halin juyayi likita guda ya sanar da su an samu nasarar dawo da numfashin Mama da mummunar mura ta tokarewa kirji sakamakon kwayoyin cuta , Sai dai ana neman jini saboda ƙarancin na jikinta da shine musabbabin kawo hargitsin ciwon nata , duk da cewa ba wannan ne karo na farko na sanya mata jikin ba kamar koyaushe a yau ma sun shaida masa sun fi son wani cikin dangi ya bada jinin fiye da na saye da ake sawa , Shi jinin sa bai zo dai-dai da nata ba haka ma na Falmata tuntuni sun san haka , Bayan likitan ya bar wajen Falmata wacce ta ji duk abunda likitan ya faɗi da faransanci tace , " ko za'a nemo wani to wanda ya yarda zai bada jinin a gwada jinin ko Allah zai sa a dace ? Yakaka wacce ta rafka tagumi kanta a sunkuye , jin haka sai ta ɗago kai , " muje a auna jini na ko zai zo ɗaya da nata , Kallonta Youssouf yayi kamar zai ce wani abu sai ya fasa , "tasso muje , yace , Da sauri Yakaka ta miƙe , kallon Falmata yayi , "Fatima yanzou zamou dawo kinji kou ? A hankali ta gyaɗa kai ba tare da ta waiga sashin da yake ba. Cikin sa'a da aka auna jinin Yakaka yazo dai-dai da na Mama jinin su B+ ne , A take aka yi duk wasu gwaje gwajen da suka dace zuwa lokacin da aka jaa jikin Yakaka leda guda , Bayan jiran tsawon awanni fiye da hudu ,zuwa ƙarfe biyu na rana aka ɗaurawa Mama jinin bayan an kaita ɗaki na musamman da suka saba zama muddin aka riƙeta a asibiti , Baki ɗayansu gajiya tare da damuwa sun bayyana a siffofinsu , tun safe babu wanda ya ci abin kirki a tsakanin su , duk kuwa da cewa Hajja ta kawo musu abincin kari  tare da kayan da zasu iya buƙata anan, kuma ta koma yin abincin dare , Ko maganar kirki basa tsawaita yi kowanne yana ji da damuwar sa da ta masa katutu , Da lallaɓa Falmata ta iya cin abincin kaɗan wanda Youssouf ne ya bata da kan shi , ba tare da ya lura da Yakaka ba , da ita ma baya ta basu tana zaune akan kujera daga gaban gadon ta riƙe hannun Mama da aka ɗaura mata jini . Ba da son ranta ba ta ɗan ci dankalin da yake sanya mata a baki tare da ƙwai, sam bata so mu'amalar su ta tsawaita a gaban Yakaka da take iya hango bayanta , " Na ƙoshi . Tace tana ture hannun sa da yake sake kawo mata dankalin , Shima bai ce ƙala ba ya janye farantin gefe , sai ta miƙa hannu ta ɗauka , ta cika shi da dankali da soyayyen ƙwai ta yunkura ta ɗauka , gaban gadon ta kai ta ja wata kujera ta ɗora akai , "Yakaka biri3 bui3 , ( Ki ci abinci ) Kallon abincin tayi , ko kusa bata jin yunwa , ganin irin yanayin da Mama take ciki ya tsinka mata zuciya , yasa zuciyarta tayi rauni , so da tausayin 'yar ta ya ci ƙarfin zuciyar , tsoron rasa ta kuma ya mamaye ta ,Sama-sama ta ci abincin . Ƙarfe biyar da rabi Hajja ta kawo abincin dare sai ta ce , "Falmata da Youssouf su tafi gida saboda halin da itama Falmatan take ciki na buƙatar kulawa da samun isasshen hutu ,  "Ita da Yakaka kuma su zauna tare da Mama a asibitin har zuwa gobe , Shawarar ta yiwa Youssouf daɗi dan haka basu jinkirta ba yace su tafi gida , ganin jikin Mama da sauki kaɗan akan zuwan su, likitoci sun ta kai kawo a kanta kuma babu laifi zazzaɓin ya sauƙa , cikin ne dai har kawo yanzu a kumbure , Falmata wacce da farko ta so tirjewa taƙi tafiya , sai da Yakaka tace mata ta tafi ta huta tunda ita ma Hajja tace bata da lafiya, Sannan fuskarta babu walwala tayi musu Sallama idanunta na kan Mama ta bi bayan Youssof wanda tun bayan da ya matsa gaban gadon Mama ya yi mata addu'a tare da sumbatar goshinta ya shafa kanta yayi ficewar sa ya tsaya daga waje yana jiran fitowar ta , Bai ce kome ba ya riƙe hannunta suka tafi , ita ma har suka shiga mota bata ce masa ƙala ba sai tunanin zuci da take yi , Bayan fitar su Yakaka ta kai kallon ta ga Hajja , "Hajja meye yake damun Falmatan ita ma ? Naji kin ce bata da lafiya amma ita bata faɗa min ba , ? Sasakai Hajja tayi tana kallon ta , "au sai ta faɗa miki tukun zaki gane ? Ji min rashin kan gado , yanzu ke Babba uwar Mama Allah baki Fahimci ƙanwar ki tana da yaron ciki ba ? Dukkanin wata nutsuwar ta Yakaka ta  tattaro ta juyo sosai ta fuskanci Hajja , muryar ta a nutse tace , " Menene yaron ciki kuma ? Ki min bayani mai kyau ni Hausa ba yare na bane Hajja ,   Kallon gefen ido Hajja tayi mata , sannan tace , " Au haka fa , to abunda nake nufi shine ƙanwar ki tana ɗauke da juna biyu , ciki na haihuwar ɗan mutum , nan da wasu watanni idan Allah ya kaimu zaki sake samun wata ɗa ko 'ya , yanzu kin gane ko Babba uwar Mama ?? Tun da ta ambaci ciki a jikin Falmata , Yakaka ta daina Fahimtar a halin da take ciki dukannin sauran bayanan Hajja bata fahimce su ba , "  Ciki a jikin Falmata ?  Kuma Youssouf ne ya yi mata ?  A lokacin mantawa tayi da cewa aure ne ya gifta tsakanin su , tashin hankalin da take ciki ji take tamkar abunda ya faru ga rayuwarta ne ya afku ga Falmata , Wani irin Kuka ta fashe da shi ta haɗa kanta da ƙarfen gadon , Shin Youssouf wanne irin mutum ne haka Mai cike da zalinci da sharri ? Bata san lokaci ya ƙure mata ba sai yanzu da tasan kome da take gudu ya faru , ƙanwarta kuma ta afkama tarkon Youssouf a karo na biyu , Youssouf yayi nasara akan ƙanwarta kamar yadda ya ci galaba akan ta , Kukan ta ya tsananta da yasa jikin Hajja yin laƙwas , karkata kai tayi tana ƙifta ido " Ikon Allah Babbar uwar Mama menene abun kuka haka ga abunda yakamata ayi farin-ciki da Samuwar sa ? Ni har jikina yayi sanyi wai kaza ta taka wuƙa , Yakaka bata kula Hajja ba , hasalima hankalinta baki ɗaya baya jikinta , ya tafi tunanin neman mafita , ita yanzu yaya zata yi ? Wanne mataki ne yafi dacewa da ta ɗauka ?  Anya tana da mafita a yanzu ? Ganin ta cigaba da kuka yasa Hajja yin shiru , hasashe take akan dalilin kukan Yakaka daga jin labarin cikin Falmata , to ko dai kishi take ?? *** Duk yadda Youssouf  ya so ya samu Falmata ta kula shi su yi ko ƴar maganar kirki ne taƙi , Tunda suka zo wanka tayi ta shige ɗakinta ta rufe ta kwanta , sai dai duk yadda ta so ya ƙyaleta ta kwana a sashinta ƙi yayi a ƙarshe ma hankalin sa ne ya tashi ya fara tambayar dalilin sauyawar ta ? Cike da fargabar ko dai Yakaka ta mata wani zance ne Amma tace masa babu kome kawai rashin lafiyar Mama ke damunta , nan ya lallaɓata suka tafi sashin sa , A nan ɗin ma zama suka yi babu wata  hirar kirki , shima da ƙarin damuwar sa da ƙira yake ta shigowa wayar sa daga Matansa waɗanda suke zuba idon ganin sa tun jiya , ya rasa kuma takamai-mai uzurin da zai basu kome ya kufce masa sau biyu yana ɗaga ƙiran su a mabanbantan lokuta yana cewa "yana uzuri ne zai ƙira daga baya ," Daga Maimounatu har Siyama sun gaza gane kan mijin nasu tun gabannin tafiyarsa turai , ga shi ya dawo ɗin ma ya zo su gan shi abu ya ta'azzara , ga shi sun gama yin duk wani shiri na tarɓar sa , Musamman Siyama da kewar sa ke walagigi da ita , tun tana daurewa har ta kai yanzu kowa ya ganta zai iya fahimtar damuwar da take tare da ita ," duk tsoronta kar wata ce ta ɗauke masu hankalin miji ,  *** Ƙiran Tafeeda ya sake shigowa karo na biyar a yau , Yana kallon wayar ta gama ƙara , kiran na katsewa ya ɗau wayar ya kashe , ya miƙe tare da kashe wutar ɗakin ya zo ya kwanta daga bayanta yayi rigin-gine . Falmata wacce duk tana jin ƙiransa da ake yana ƙin ɗauka , ta kuma fahimci wata sabuwar damuwar da shima yake ciki , sai ta ji tausayin sa ya kamata , ko babu kome a gurinta shi mutumin kirki ne , managarci Mai kyaun hali da kyakkyawar zuciya ,  sai ta juyo a hankali ta ɗaura kanta akan ƙirjinsa ta rungume shi da hannun ta guda, tana jin lokacin da yayi ajiyar zuciya mai ƙarfi . Cikin dare bacci ya ƙauracewa idanun Youssouf tunaninnika sun masa yawa , yana son ya san halin da Mama ke ciki yasan kashe wayar da yayi ma a halin yanzu kuskurene tunda yana da marar lafiya a asibiti , Dan haka ya miƙe zaune ya ɗau wayarsa tare da kunna ta , kan layin Hajja ya danna ƙira yana kallon agogo wayar da ya gwada masa ƙarfe ɗaya saura mintuna biyar , Yasan cewa dare yayi sosai amma ya zama dole ya san halin da ɗiyar sa ke ciki tun bayan barin su wajen ta , da kuma yadda zata kwana , A can wayar ta ɗau ƙara , yaji alamun shigar ƙiran , Muryar da ta doki kunnuwan sa ya sanya shi miƙewa tsaye , yayi taku kaɗan , yana waiwayen Falmata , " Mai wayar tana bacci ,    cewar Yakaka da ita ta ɗau wayar Hajja saboda ƙarar wayar kar ya tayar da Mama da ta samu bacci da kyar bayan kukan ciwo da take yi , tare da rikicin neman Iyayenta .   " Yaya jikin Mama ? Yace , yana fitowa daga ɗakin zuwa falo domin kada ya tayar da Falmata daga bacci , Miƙewa tayi daga kujerar da take kai , tana jin tsanar sa na sake bijiro mata da jin sautin muryar sa  , " Youssouf     Ta ƙira shi , bata sauƙe mumfashi ba ta ɗora da cewa , "ina batun mu ? Kar ka manta da abunda na faɗa maka muddin kana son cigaba da ganin farin-cikin iyayen ka sannan.... Katse ta yayi , " yaya jikin ɗiya ta nake tambayar ki ? Ke baki da tounani ne ? Baki ganin halin da Mama take ciki ? Ba yanzou bane lokacin yin wannan maganar kiyi hakuri don Allah . " Yanzou ki tada Hajja daga barci ki bata wayar zan tambaye ta kan lafiyar  ɗiya ta , Ƙit ! Yakaka ta kashe wayar har ita yake ƙira marar tunani ? Akwai marar tunani da ya wuce shi ? Duk sanadin waye suke cikin halin da suke ciki a yanzu ? Da bata haɗu da shi ba zata haifi Mama ne ? Ko kuwa yana nufin shi da ya gudu ya barta da cikin Mama ya fita ƙaunar Mama ɗin ne ? Yana da sani ne ko kaɗan akan irin wahalar da ta shiga na kwana a rumfar kasuwa tare da cikin Mama a jikinta ? Guntun tsaki tayi tana komawa ta zauna a kujerar da ta tashi ,   ta shafa kan Mama wacce take baccin zoma tana ɗan nishi kaɗan-kaɗan , duk da cewa an ƙara mata jini leda guda amma har yanzu ƙafa da hannunta fari sol alamun rashin jini tausayinta yana sake kama ta , ko runtse bata runtsa ba , tun lokacin da Hajja ta faɗa mata cikin jikin Falmata damuwarta ta sake ninkuwa , Duk dogon nazarin nema mafita da tayi hankalinta yaƙi amincewa da ta ƙyale Youssouf ya cigaba da zama da ƙanwar ta ta gwammace ya saki Falmata su koma Nigeria tayi rainon cikin ta haihu idan yaso su ɗauko abunda aka haifa a kaiwa iyayensa tunda shi da Falmata aure suka yi , Dole iyayensa zasu riƙe abunda ta haifa , ita kuwa Mama 'ƴar ta ce da suka haifa ba tare da aure ba ta san iyayensa baza su riƙe Mama ba , Mama zata kasance tare da ita . ** Youssouf ya ji yadda ta katse ƙiran ba tare da ta bashi amsar da yake son ji ba , sauƙe wayar yayi bai sake ƙira ba ya juya ya koma ɗakin , Zama yayi a bakin gado , cikin ransa rikicin da Yakaka ta zo da shi ya kai matakin ƙure shi, ya fara neman mafitar yaya zai yi da Yakaka domin kuwa ko a mafarki ba zai yi mata yadda take so ba , ya saki Matarsa akan wanne dalili ? Aurensa da Falmata aurene da sai mutuwa ce kaɗai zata raba su , Yana son matar sa , yana ƙaunar ta ,yana tausayin ta , ya kuma shirya tsaf domin zamar mata bango abun jingina , idan ya rabu da ita taje ina ? Waye zai jiɓanci lamarin ta ? Wa suke da shi a duniya jigo ?  Daga ita har Yakaka masu rauni ne domin kuwa mata ne  tayaya zai sau aurenta ?  Alhalin ga zuri'a a tsakani Allah ya fara basu , dangantakar su ba mai yankewa bace har abada ba zai rabu da ita ba ko da kuwa ace ita da karan kanta ta nemi da ya sake ta ba zai aikata hakan ba , bare wasu mutane daban da ba sune suke riƙe masa da igiyoyin auren sa ba  , Fatima Zara matar sa ce har a lahira baya fatan rabuwar su . Zai roƙi Yakaka da tayi hakuri ta yafe masa duk wani laifi da take zaton ya yi mata , tare da Alƙawarin kula da hidimar Rayuwar ta muddin zata yadda ta cigaba da rufe asirin tsakanin su daga sauran mutane , ciki har da Falmata da Mama idan ta girma . sannan tayi haƙuri ta koma Nigeria ta samu miji tayi aure shi zai tsaya mata a wannan gaɓar . muddin kuwa taƙi yadda da tayin salama , bai iya hasashen yadda ƙarshen lamarin su zai ƙarƙare , bai san ba gurin hukuntata akan yunƙurinta na raba shi da matar sa ko zai iya yi mata sassauci Albarkacin Mama ba? abunda ya riga ya sani ne tun a ranar farkon ganin sa da ita ba soyayya ce ragamar tarayyar su ba illa musiba tare da sharrin shaiɗan da shi ya faɗawa a ciki , ita kuma ta gagara tsamo sa a madadin haka ma sai ta zama abokiyar taya shi ,ashe idan haka ne itama da nata laifin , Zai yi kome zai kuma jure kome domin ganin ya cigaba da rayuwa da matar sa da 'ya'yan sa , A hankali ya hau gadon ya rungume ta tsam a jikinsa , runtse ido tayi hawayen da suka taru mata suka zubo , tun daga tashin sa ta ji shi , ta ji wayar sa da Yakaka , Wanne irin sirri ne a tsakanin su da suke ɓoye mata basa so ta ji ? Jikinta yana bata rabuwar su da ita da Youssouf ta zo kusa. Washegari Tunda tayi sallar asuba gari yayi haske ta shiga kitchen duk kuwa da Youssouf ya so hana ta amma ta dage , "bai kyautu ba kuma Hajja ta dawo daga asibiti tayi mana girki zan iya ba abu mai wahala zan dafa ba kawai pasta ne zan yi , tace da shi . Ba yadda ya iya saboda gaba ɗaya ta koma mishi kamar farkon auren su , sai janye jiki take da shi ,tana ƙin kallon sa , bata tsawaita zance da shi Bayan ta gama girkin ta zuba ta rufe , ta zo ta wuce shi a falon yana zaune ba tare da tace masa kome ba , Da ta shiga ɗaki wanka tayi ta koma ta kwanta a gadon ta saboda tun ƙarfe ɗayan dare rabon ta da baccin kirki , lokacin da ta ji wayar da suka yi , tana kwanciya bata daɗe ba bacci ya ɗauke ta Youssouf  da ya gaji da jiranta ta zo suyi karin kumallo , tashi yayi ya leƙa ɗakin nata , A gado ya hangota tayi luf tana baccin ta , ransa yayi sanyi da yaga tana bacci sosai haka , a hankali ya taka zuwa cikin ɗakin , Zama yayi a bakin gadon yana ƙarewa fuskarta kallo , ƙaunar ta na sake fisgar shi , gani yayi ta fi yi masa kyau idan tana bacci , Kamar motsi ya ji an taɓa ƙofar falon , dan haka ya miƙe ya fito yana dube-dube , sai dai bai kai ga ganin kome ba , tsayuwa ya cigaba da yi a harabar gidan ya zura hannu a aljihu yana tunanin zuci , "yana son zuwa Maraɗi ko domin iyayensa , amma tsoron abunda zai tarar a can ya hana shi samun ƙarfin zuwa , Ciki ya koma inda ya tarar wayar sa da ya ajiye akan kujerar da ya tashi tana ƙara , Zuciyar sa ta buga da ƙarfi ganin Mai ƙiran nasa da ba kasafai ta cika yin ƙiran waya ba , sai fa da Babban dalili ko kuma idan shi ya ƙira domin gaishe ta , "Adda Ammi ce Babbar yayar su baki ɗaya da take aure a jahar Damagaram , Har wayar ta tsinke bai ɗauka ba saboda fargaba , amma bai jinkirta ba ya bi bayan ƙiran da hanzari , ** Daga cikin motar ƙirar Honda Accord  da take tafiya da matsakaicin gudu akan titin Boulevard Mali Véro , Hamshaƙan matan su biyu masu kamanni ɗaya suke zaune , ɗaya tana daga gaba Babbar tana baya , ta gaban ta ɗan waiga kaɗan , lokacin da direban ya karya kan motar zuwa cikin unguwar da take gefe da su , "Adda Ammi kadda kice mini ke ma Youssoufa bai ɗau ƙiran ki ba ? Zata yi magana wayar ta ta ɗau kiɗan shigowar kiran sa , " ga shi ya biyo sawun ƙiran ,    Tace ba tare da ta ɗaga ƙiran ba , Tafeeda wanda shi yake jaan motar ya juyo kaɗan kafin ya maida hankalin sa ga tuƙin yana cewa "ai ga gidan can ma mun iso Adda Ammi , Duk suka zubawa gidan ido ta cikin gilashin motar suna kallo ,bayan ya dai-daita tsayuwar motar , suna shirin fitowa lokacin da suka ga an buɗo ta ƙaramar ƙofar gidan a hankali an fito , Su dukkanin su wara ido suka yi suna kallon sa da Mamaki , " Mouhammadou ? Tafeeda ya ƙira sunan sa da mamaki a muryar sa  , suna ganin yadda yake dube-dube yana sauri , ya miƙa kan titin unguwar da babu kowa shal , sai fa giftawar motoci jifa-jifa , ba tare da shi ya gan su ba saboda gilashin motar da yake da duhu , Shiru ne ya gifta tsakanin su , kafin Ubbo ta ce "Tafeeda ka ce mouna babu wanda ya san da tabbatuwa lamarin nan sai kai ɗai ?  Sai kouma mu da yanzou ka taho da mu , to Yaya anka yi mouhammadou ya iso nan ? Ko kouwa shi Youssoufa ya ƙiraye shi ? Cike da nazari Tafeeda ya nisa , "Adda ni bansan kome game da wanzuwat shi ba , wataƙila Youssoufa ya ƙiraye shi , sai dai nafi zaton zuwan kan sa yayi ɗauke da wani ƙudiri nashi na daban , Duk suka sake yin shiru a motar , bayyanar Mouhammadou a boyayyen gidan Youssoufa na sirri ya sanya su a ruɗani , Bayan iyayen su da suka san maganar zaman Youssouf da mace har ma da ɗiya ba ta aure ba a ta bakin wasu mutane , Tafeeda shine mutum ɗaya tal da yasan haƙiƙanin gaskiyar lamuran , shine kuma ya yi ta ƙoƙari wajen ganin ya wanke Youssouf , ya dunga neman Youssouf da ya dawo su fuskanci matsalar su maganceta tun kafin duniya ta ɗauka . Amma daga baya  sai Youssouf yaƙi ba shi haɗin kai , wannan dalilin ne ma ya sa shi dole ya samu yayun Youssouf ɗin Adda Ammi , da Ubbo da su ma suke cikin tashin hankali jin cewa ɗan uwansu yana can America tare da karuwa da 'yar su , Shi yayi musu bayanai na haƙiƙanin gaskiyar kome cewa ba fa zaman dadiro Youssouf yake yi ba amren yarinyar yake yi daga ƙasar Nigeria wacce kuma ƙanwace ga ainahin uwar yarinyar da ya yiwa ciki ba ta hanyar aure ba ta kuma rasu a wajen haihuwar 'yar . Ba ƙaramin baƙin-ciki suka shiga ba da jin irin ta'asar da ɗan uwan su ya aikata , har kuma yake da tsaurin idanun cigaba da yin yadda ya ga dama , Dan haka suka tsaida shawarar muddin Youssouf ɗin ya dawo su zasu yi takakkiya zuwa gidan da ya ɓuya yake yin rashin gaskiya , su kuma sanya dole ya saki amren yarinyar da yake riƙo tare da haɗa ta da ɗiyar su koma da ita can ƙasar su , su basa yadda ya gurɓata musu sunan zuri'a da masarautar su , ba kuma zasu amince ya kawo musu baragurbin ɗiyar sa ba , bare wata matar da bata da masauƙi a tsakanin su , wacece ita da zata zama sanadin ɓacin ran iyayen su , ta kuma samu damar zama matar ɗan uwan su Yarima sarkin watarana ?? Adda ammi ta ɗau wayar ta tana sake ƙiran layin Youssouf dai-dai lokacin da taxi ɗin da Yakaka tayi shata , ya ajiyeta a ƙofar gidan ta bashi kuɗin sa , Ta kama hanyar shiga gidan hannun ta riƙe da kulolin abincin da ta dawo da su daga asibiti , da kyar take taku saboda tsabar gajiya da bacci da ya cika mata ido , Adda Ammi tana jin Youssouf ya ɗaga wayar bata tsaya amsa gaisuwar sa da yake yi mata ba cikin dakakkiyar muryar ta tace da shi , "Youssoufa ga munan ƙofar gidan ka , ka hito ka yi mouna jagora , Da 'yar ruɗewa cikin muryar sa lokacin da yake miƙewa yana barin abincin da ya fara ci yace "Adda ai bani gida maraɗi ba kouma na tahoue , ina Niamey ne wajen aikina , "Na sani ƙofar gidan ka na niemey ɗin nake magana ko kouwa baka hitowa ka mouna jagora sai mu shiga da kanmu ? Fitowa yayi hankalin sa a tashe ya nufi ƙofar gidan ko takalma babu a ƙafarsa  , A harabar gidan ya ci karo da Yakaka wacce take shigowa , kallon juna suka yi kowannen su ransa a ɓace , ya gota ta kai tsaye ya buɗe ƙofar gidan idanunsa suka sauƙa akansu duk ukun suna fitowa daga motar , Yawun bakin sa ya ji ya ƙame , ya rasa halin da yake ciki takamaimai  , , da murmushin yaƙe ya ƙaraso gaban su , ya ɗan sosa ƙeya bayan ya rage tsawo ya shiga gaishe su , Sama-sama suka amsa suna binsa da kallo ganin yadda duk yake a firgice da alamun rashin gaskiya , "Bismillah, yace da su yana yin gaba , ba tare da ko sau ɗaya ya dubi sashin da Tafeeda yake tsaye ba saboda gudun yadda zata kaya a tsaƙanin su da ya riga ya san cewa shine ya haɗo masa wannan gangamin , Da shigar su harabar gidan yayi nufin kai su sashin sa , sai dai tsintar maganar Adda Ammi yayi tana tambayar sa ina matar gidan ? Cikin dakiya ya waigo , "tana ciki , yace a takaice yana kallon ta , "to ai wajen ta yakamata mu shiga duk muyi maganar da take tafe da mu  , Ɗan jim yayi yana kallon ta , cikin shakku , sai dai yadda tayi maganar cikin lumana ya sa ya wuce gaba zuwa sashin Falmata suna bin bayansa , Zuciyarsa cike da fatan samun masalaha akan koma menene , fatan sa Allah yasa zuwan su ya gyara kome , Suna shiga falon suka tarar da Yakaka a zaune daga ƙasa tana hutawa tare da jiran shigowar Falmata da take zaton ko tana wajen Youssouf zuciyarta ɗauke da ƙudirin fara sanar mata da kome a yau , Shigowar su ya sa ta miƙe , fuskarta kadaran-kadahan ta gaishe su , Shi Tafeeda bai amsa ba , Ammi da Ubbo ne suka amsa a taƙaice suna ƙare mata kallo sama da ƙasa , zuciyar su na shaida musu wannan me kama da asbinawan ce ta sa ɗan ouwan su kaucewa hanya ?? Ratsawa tayi zata wuce ta bar su Ubbo ta dakatar da ita , "baiwar Allah dawo nan , kou ba ita ce  matar gidan ba ?    ta juya akalar tambayarta ga youssouf Da sauri Youssouf ya girgiza kai ,    "Ba itta ce ba , To ita wannan wace ? Adda Ammi ta tambaye shi a ciki ya amsa , "yal ouwatta ce , .ubbo tace "itta ina tai ? " bacci take , adda domin Allah muyi duk maganar da zamu yi ni da ku , "Ke Adda Ummi ta buɗe murya wajen ƙiran Yakaka wacce har lokacin take rakaɓe daga gefe a tsaye , "ki tai ki tado mouna da 'yal ouwakki ku taho tare , Yakaka bata san me suke nufi ba hausar tai mata nisa dan haka ta tsaya tsam tana kallon su ta ƙasan ido , Youssouf da yanayin Ammi ya fara ɗarsa masa tsoro a rai , ya nunawa Yakaka ɗakin da Falmata take ciki ,yace " Fatima tana ciki ki ƙira ta , A hankali Yakaka ta tura ƙofar ɗakin Falmata da har kawo yanzu baccin ta take yi , Ta ƙarasa bakin gadon a hankali ta dafa ta , "Falmata , Falmata , ta ƙira sunan ta tana ɗan jijjigata , Buɗe idanunta da suka yi mata nawi tayi , sai kuma ta ware su da sauri ta miƙe zaune tare da riƙe hannun Yakaka da take hango ta dusu-dusu , " Yakaka kece ? Ina Mama ? Ya jikin nata ? Ta samu sauƙi ? Tayi bacci ? Bata yi kuka ba ko ? " jikin Mama da sauƙi na baro ta tana bacci , Yanzu muje falo kina da baƙi , " Baƙi ?su waye  ? mu babu wanda yake zuwa wajen mu ai ? "wasu mata ne ina ga ƴan uwan sa ne , Yakaka tace tana miƙewa tsaye , A hankali Falmata ta kai hannu ta laluɓi gilashinta ta sanya a fuskar ta , bayan ta ɗora hijabi akan doguwar rigar jikinta , Tare suka fito falon yatsunsu cikin na juna  , Har ƙasa Falmata ta durƙusa ta gaishe da matan da ta tarar da ƙamshin su ya cika falon , sannan ta gaishe da Tafeeda , Sai tayi shiru jin yadda suka amsa mata a cike da ginshiri , "wannan ce matar taka ? Uwar 'yar taka ? Wannan kuma 'yar uwarta ? Adda ummi ta tambaya tana nuna Falmata da Yakaka da hannun ta a walaƙance , "Eh , ah ah , eh ita ce Matata Fatima , Kallon sa su duka biyu suka yi jin yace "eh ya kuma ce "Ah ah , Gyara zama tayi ta matso kusa daga kan kujerar , " ke yarinya kina jina ?   Falmata wacce ta fahimci da ita ake , ta gyaɗa kai a hankali bayan ta fuskanci inda take iya ganin Matar da take mata magana sosai , " daga ina kike ? Su waye iyayen ki  ? daga Falmata har Yakaka zuciyoyin su suka buga , Sai Falmata ta sake matso Yakaka tana riƙo Hannun ta , A hankali Yakaka ta sauƙe ganin ta akan Adda Ammi , " Mu 'yan gudun hijira ne a ƙasar Nigeria, kuma iyayen mu duk sun rasu , Ƙutawa tayi tana gyaɗa kai cikin buɗaɗɗiyar Muryar tace " kin san Youssouf wanene ? Girgiza kai  Falmata tayi alamun "ah ah ,    " shekarar ku nawa kuna amre ? Youssouf wanda ya fara hango tsoro a fuskar Falmata tare da hasasho inda Adda Ammi zata ƙarƙare maganar ta ya yunƙuro da nufin katse ta " Adda Ammi  .... Da hannu ta dakatar da shi , "Youssoufa ba kai nake tambaya ba , "yarinya shekarun ku nawa nace da Amre ? "shida ,    Falmata tace cikin siriryar muryar , zuciyar ta cike da son sanin yau wacece agaban ta ko dai mahaifiyar Baban Mama ce ?? Muryar ta ya katse mata tunani, "kin taba ganin wanni daga cikin dangi nashi ya zou inda kuke ? Ko kouwa ku ya taɓa sada ku da dangin sa ? Shiru Falmata tayi , "kin san dalili ??  Bata jira amsar Falmata ba ta ɗora da cewa , "sabadda kama dagga kan iyayensa da mou 'yan ouwansa har zouwa kan dangin da masarautar mu zouwa kan mutanen jahar mou baki ɗaya ba mou san da amren kou ba , "Youssoufa ɗan Sarki ne , Yarima ne shi , yana da iyayen sa suna raye mu yayyensa ne , yana kouma da ƙanne , sannan yana da matan amre har biyu da ɗiyar sa , "duk baki san mou ba , a yadda ɗan'ouwansa kuma abokinsa ya buncika mouna ya amre ki ne tare da ɗiyar yal ouwakki da ta haifa ba tare da sun yi amre da shi ba shigiyar ɗiya, ya zo nan ya ɓoye kou , yana rayuwar sirri da kou , kin raba tsakanin sa da matayensa , kin ɗauke hankalin sa daga aikin sa , bashi da watta hidima sai taku ke da ɗiyar da gurɓatatciya ce shin yarinya baki gudun jefa rayuwarki ga hargitsi maigirma ? Cikin wata irin murya Falmata ta ɗamƙi hannun Yakaka ta jijjiga ta tare da cewa " Yakaka kiyi magana mana , kina ji fa an ƙira Mama shegiya , shiru Yakaka tayi tana jin yadda wani abu ya zo mata ƙahon zuci ya takore , ko motsa laɓɓanta ta gaza , Juyawa tayi wajen da Youssouf yayi suman zaune akan shamtar sa da Adda Ammi tayi , "Baban Mama ka ji wai Hajiya yayar ka tace Mama ba 'yar aure bace , ka faɗa musu gaskiya yadda ka faɗawa Baba prof lokacin auren mu dan Allah, Hawayen da suka cika gurbin idanunta suka sauƙo , ta matso gaban su , " Hajiya dan Allah ko da ni baza ku karɓeni ba kuyi haƙuri ku karɓi Mama kar ku ɓata mata asali , Mama yarinya ce marar lafiya dan Allah kar ku .... Tsawar da Ubbo ta daka mata ya sanyata yin shiru ,, "ke yarinya raba mu da ƙazanta ,yadda kuka zou tare hakka zaku kouma tare , mu karɓi ɗiya mu tai da itta ina ? Muyi me da itta ? Mu 'yan nasaba ne , ɗiyan asali ɗiyan halak ba zamou taɓa yadda da zouwanta cikin mou ba ai daman ɗiyan zina na uwattai ne , can zaku koma da itta , Da rishin kuka Falmata ta miƙe tsaye ta tsaya akan su , "ƙarya kuke yi Yakaka ba ƴar iska bace bata taɓa zina ba , dan haka Mama ba shegiya bace , Juyawa tayi ta ɗago Yakaka da ruwan hawaye ya jiƙa mata gaban riga , ko kusa bata san wannan ranar da zasu shiga tozarta ita da "yar uwar ta a sanadin kuskuren da ta aikata zata zo ba , Kuma bata so ba wasu suka riga ta sanar da Falmata ta irin hanyar da ta samar da Mama ba , jijjigar da Falmata ta yiwa kafaɗunta da ta riƙe duk biyu shi ya tsorata ta , "Yakaka kina jina ki je gaban su ki faɗa musu ƙarya suke miki sharri suke muku ke da Baban Mama ba zina kuka yi ba , ki faɗa musu Mama ba shegiya bace , ki ce musu ƙarya suke yi , Mama ƴar halak ce kamar su , Ta karasa zancen tana fashewa da kuka , Kukan da ya hargitsa duk wata guntuwar nutsuwar da ta ragewa Youssouf , ya miƙe a ɗimauce , lokacin da muryar Yakaka ya ratsa wajen , " Gaskiyar su ne Falmata , Mama shegiya ce , ba muyi aure ba ni da Baban Mama muka haife ta , tamkar an harbi ƙwaƙwalar ta haka Falmata ta ji zancen , sai ta wara idanun ta fes akan fuskar yar uwar ta muryar ta babu ƙarfi irin na ɗazu illah tsantsar tashin hankali ta ce  " Yakaka tsoron su kike ji ? Dan kina tsoron su shine kema zaki ƙira Mama shegiya dan kawai bakya son ta ? , sai ta tunkuɗe ta baya  , ta wuce kai tsaye wajen Youssouf da ƙafafun sa ke karkarwa ta tsaya daf da shi ta ɗaga kai tana hangen farar fuskar sa  "Baban Mama ka cewa Yayar ka ƙarya take ,  ka faɗa musu kai mutumin kirki ne bazaka cutar da Yayata ka ɓata asalin Mama ba ? Ka faɗa musu ba zaka yi zina da Yayata kuma ka aureni ba . hannun sa dake rawa ya miƙa ya rike kafaɗar ta  , sai dai hannun sa yana sauƙa a jikinta ta doke hannun da wani irin matsanancin fushi , tace "kaima zaka ce gaskiya ne ? Eh ? Ubbo wacce abunda Falmata take yi ya fara bata haushi a ganin ta tsaurin idanun Falmata ya wuce iyaka da har take ƙaryata su kai tsaye ,ta kuma tsare Youssouf ɗin a gaban idanun su  dan haka sai ta miƙe tsaye ta ƙaraso wajen , Ta fuskance shi tana cewa " Youssoufa menene haka nake kallo ? Macce ke tsare gaban ka Youssoufa ? A gaban ka take ƙaryata Adda Ammi ? Ka sake ta Youssouf a yanzou , ka sau amrenta nace wacece itta da bata wuce bayun mu ba ? Da dukkanin Fushin sa ya juya gare su   muryar sa da Amo mai ƙarfi laɓɓansa na karkarwa yace. "Adda Ammi, Adda ubbo , Tafeeda ,  domin Allah ku tafi abunku , ku fita dagga Rayuwa ta , Rayuwata tawa ce ni ɗaya ba tare da ku ba , duk kome nayi a cikin ta domin kai na ne , " ba zan saki Matata ba haka kouma ba zan rabu da ɗiya ta ba , naji ban samar da Mama ta halastatciyar hanya ba  , amma ina ƙaunarta fiye da yadda nake kaunar kaina , ni nake da laifi Mama ita wankakkiya ce tsaftatatciya , "ba zan danganta Mama da ku ba asalinta ya tsaya ne daga kaina ni kaɗai , ba zan raɓa ta da ku ba ,  samuwar Mama a wajena wani kaddara ne Maigirma daga ubangijina  ,don Allah Adda ku tafi nace , "to maras kunya fitsararre , idan kai ka zare mu dagga rayuwar ka mou ba mou fita ba , asalin mu gouda da kai sannan akwai hakkin 'yan ouwantaka da na iyayen mu akan ka  , Ubbo tace haka , Bata saurare shi ba ta juya ga Falmata wacce ta durƙushe a wajen tana wani irin kuka marar sauti , "ke yarinya tunda baki da alkunya  ku tattara yanzou ku fita zouwa wani wajen cen ,  ku tafi kuyi nesa da ƙanina shi ba tsaran amren kou bane ɗiyan matsayitta masu gajeren assali ƴaƴan titi.... Kalamanta sun ƙona zuciyar Yakaka , dan haka ta tako gabanta tana jin duk wata shakkar su na ficewa daga ranta tace , " Ya isa , Ya isa nace Ya isa kar ki zagi iyayen mu , da basa raye a duniya ,  ko daman baki faɗa ba Falmata ba zata cigaba da zama da azzalumin ɗan uwanku ba , wanda tushen sa da asalinsa tare da girman da kuke fariya da shi bai katange shi ba daga aikata alfasha , kamar yadda kuka faɗa ya zama dole ya saki ƙanwata ya kuma ba ni ɗiya ta , " Nima bazan taɓa yadda ta zauna atare da ku ba , idan kun so a yau ku ɗora shi ya zama sarki , har abada Mama baza ta sake nuna shi a matsayin Uba ba , Takawa tayi ta ƙarasa gaban Youssouf , idanunta jazir da ɓacin rai tace " ka saki auren Falmata na sake maimaita maka , ka kuma fita daga rayuwar mu Youssouf ... Assalamu Alaikum masu karatu , da fatan duk kuna lafiya ?? Wannan shafin kachokam ɗinsa tukuici ne ga duk wasu masoyan MHR a duk inda kuke alherin Allah ya iske ku ,  ina ƙaunar ku domin Allah 😍❤ Nagode [11/29/2019, 1:17 PM] +234 806 600 1491: MAFARI ( Hargitsin Rayuwa ) Umm'muaz 43 Ƙiran wayar Youssouf da aka yi ƙarar ita ta ratsa shiru mai ɗauke da tashin hankalin da ya biyo bayan martanin Yakaka , Baya cikin nutsuwar sa ya dubi fuskar wayar da take riƙe a hannunsa , ganin wacce take ƙiransa ya sa zuciyar sa ta tsinke , Hannunsa na rawa ya ɗaga ƙiran wayar da ya zarce da sanya ta a hands-free batare da ya ankara ba , Muryar Hajja ciki kuka ta karaɗe falon , da take cewa "Babban soja , ku zo Dan Allah, ku zo wajen Mama ku ga jikin nata , jikin Mama babu daɗi... Rige-rigen ficewa daga falon aka yi tsakanin Youssouf ,Yakaka da Falmata  da babu wanda ya saurari kansa bare waninsa burin su kawai su isa wajenta , Kuma a tsakanin Falmata da Yakaka babu wacce ta nufi motar Youssouf da ya shiga ya tayar dukkanin su biyu kai tsaye mafitar gidan suka nufa , Suna fita ya sha gabansu da Motar ,"ku shigo ,   Yace da wata irin murya Dukkanin su a lokacin ganin Mama shine burin su , dan haka suka shiga motar ya jaa da gudun gaske , A lokacin hawayen fuskar Yakaka da Falmata sun ƙafe kamar yadda yawun bakin su ya ƙafe ya daƙile fitowar wata kalma daga gare su , bayan addu'o'i babu abunda kowannen su yake yi a zuciya Suna ficewa daga layin gidan motocin da suka yi jerin gwano su kimanin guda biyar suka shiga layin . Gudun da yake yi ya wuce ka'idar tuki , kiyayewar Allah kaɗai ta kai su asibitin , ba inda ya kamata ya ajiye motar ya ajiye ba , bai ko lura da securities da suke masa magana ba , ya fito daga motar sauƙar ƙarfar sa akan titin da ya ɗau zafin rana shi ya ankarar da shi cewa fa ko takalma babu a ƙafafunsa , da gudu-gudu suka nufi ɗakin da suka san Mama tana ciki suna rige-rigen kutsa kansu , Turus suka yi ganin babu kowa akan gadon nata , da sauri ya fita suka bi bayansa , ma'aikaciyar jinyar da ya fara cin karo da ita zata wuce ya tambayeta ,"ina ɗiya ta ? Ta san shi sosai a saboda yadda suke yawan zaman asibitin da kuma kasancewar sa babban Mutum , sai ta nuna musu ɗakin da aka mayar da Mama wanda yake daga ciki sosai , Bai saurari me zata sake faɗi ba ya nufi inda ta kwatanta masa da sassarfa , Bankaɗa ƙofar ɗakin yayi ya danna kai su Yakaka suna bin sa ba tare da sun bi ta kan Hajja wacce take tsaye daga bakin ƙofar tana sharar hawaye da gefen mayafin ta ba , Shigar su ya zo dai-dai da lokacin da likitan yake zare trach tube ɗin da yake fuskar Mama , Da gudu Youssouf ya ƙarasa ya ratsa ta tsakankanin Likitocin da suke zagaye da ita , fuskokin su cike da Alhini , Ya tarairayo ta bayan ya zauna a bakin gadon ya ɗagota lokacin da take jaan wani irin numfashi mai tafe da gurnani ciki-ciki , idanunta a buɗe akan fuskar sa  , Hannun sa ya kai yana goge mata tsinkakken yawun da yake zuba a bakin ta , muryar sa tana karkarwa yake kallon likitocin yana cewa, " Doctora yaya hakka ? Kuyi wani abu mana , Mama tana hakka alhalin  kuna tsaye ? "Mama, kar ki barni ki dubeni Mama , ya ƙira ta da wata irin muryar yana jijjigata a jikinsa ganin yadda idanunta suka yi sama , numfashin da take kokawar riƙewa kuma ya ƙarasa barin jikinta , dukkanin wasu jijiyoyin jikinta suka tsayawa aiki , kamar yadda zuciyarta ta tsaya chak daga barin bugawa na har abada . Da gudu Yakaka ta ratsa tsakanin su ta kai hannu tana riƙo hannun Mama da yayi wani irin sanyi ƙalau ya sake , "Mama tashi mana , me ya same ki haka ? Innalillahi wa inna ilaihi raji'oon .   Tace da kuka a muryar ta , "Mama , Falmata ma ta ƙira ta lokacin da ta ƙaraso gurin idanunta basa gani sosai Amma tabbas a yau tana iya hange gefen Fuskar Mama tar-tar , shafa kanta tayi da yake rungume a kirjin Babanta "Mama meye ya same ki ? Ki tashi Mama , kin ga fa Mamar ki ta asali ta dawo zata rayu da ke , Mama baki ko mata magana ba , bata ji muryar ki ba shine kuma za ki zama haka ? Mama ki tashi  , Ta ƙarasa maganar tana jijjiga su ita da Youssouf , Kafaɗar Youssouf Babban likitan ya dafa , yana cewa " Innalillahi wa inna ilahi raji'oon , kuyi hakuri duk wani ciwo na safiyya ya warke , ta komawa ga Ubangijinta , dukkan wani mai rai mamaci ne kuyi haƙuri , kuyi haƙuri , kuyi addu'a Baya yayi a hankali yana kaucewa ganin tashin hankalin da yake ƙwarar idanun su su ukun ,da suke kallon sa  zuciyar sa cike da tsantsar tausayi , tabbas mutuwar abunda ka haifa akwai ciwo , ciwo kuwa mai raɗaɗin gaske , ɗaya bayan ɗaya likitocin suke ficewa daga ɗakin suka bar guda biyu kawai a tsaye , Jikin Youssouf babu inda baya rawa , ya zaro Mama daga ƙirjinsa yana kallon fuskar ta yadda kan ta ya tafi galau , Ya sa kukan da yake riƙewa fisge masa ,  sai ya fashe da kuka mai ƙarfi ya mayar da ita ƙirjin sa da yake wani irin bugu da matsewa tamkar ana daure masa jijiyoyin dake gudanar da jini ta cikin sa , amon kukansa ya sa Hajja shigowa ɗakin , cikin ranta tana aiyana inda ake gudu nan aka zo aka tsaya , Mama ta rasu , Tun-tuni ta ga Alamun mutuwa a tare da yarinyar tunda jikin ya birkice daman ranta yake kai-kawo , Allah sarki mutuwa bata a shekaru , bata barin ƙarami ta ɗau babba domin wai ta jinkirtawa girman sa , ita lokaci kawai take jira , ko ɗan da yake cikin mahaifiyar sa tana ɗauka , Falmata wacce hankalinta ya kasa amincewa da mutuwar Mama kamar yadda likita ya faɗa , ƙarasawa tayi ga Yakaka wacce ta zube guiwar ta biyu a ƙasa ta kifa tafukanta biyu akan fuskarta , kuka take marar sauti , illahirin jikinta rawa yake sai ta kai hannu ta dafa ta , a lokacin da Hajja ta nufi wajen Youssouf , da muryar dake bayyana tsoro da tashin hankalin da me ita yake ciki tace , "Yakaka , ki tashi , ki tashi ki karɓi Mama mu tafi , mu tafi da ita Yakaka , ko kin manta da Alƙawarin da muka mata tun tana ciki ? Cewa ni da ke zamu kula da ita Yakaka , zamu bata kariya yaya kuma kina gani Mama zata tafi ta bar mu , ? Alhalin ...Ya.Yakaka ki tashi nace kin san fa mu uku ne kaɗai a duniya Dan Allah kar Mama ta mutu , Mama kar ki barni mana , yaya za ki min haka Mama ? Bayan nayi alƙawarin zaki warke Mama . Kuka ne ya ci ƙarfin ta har tana shiɗewa numfashinta ya fara yin sama-sama Da sauri Yakaka ta rungumeta kukan ta yana daɗuwa ta riƙe fuskar ta , "Falmata kiyi addu'a , kice innalillahi wa inna ilahi raji'oon , mu da Mama duk Allah ne ya yimu , ya bamu rai da muke rayuwa da shi , kuma shine ya hallicci mutuwa ya sa ta zama mai zare rayukan mu idan lokacin da ya kayyade mana na rabuwar mu da ruhin mu yayi , da ni da ke da Baban ta duk Allah ya fi mu sonta kiyi mata Addu'a Falmata , Da ƙarfi Falmata ta rungume Yakaka wacce ƙarfin hali ne kawai take yi domin kadda Falmata tayi rauni dayawa ,ita abunda take ji bata taɓa jin makamancin sa ba wani abu take ji mai ɗaci yana kai kawo a tsakanin zuciya da maƙogoron ta , gaba ɗaya ranta cike yake da duhu da take iya ganin duhun har ga idanunta , Hajja tana ƙarasawa ga Youssouf ta shiga bada baki da tunasarwar da ake yiwa wanda aka yiwa mutuwa , itama sharar hawaye take zuciyarta cike da tausayin su , tana kimanta irin zogin da zuciyoyinsu ke ciki kan mutuwar ɗiyar su , Sun ɗau mintoci kusan goma a haka cikin halin ɗimuwar jin zafin mutuwa kafin likitocin biyu su nemi da ya basu Mama zasu zare duk na'urorin su da suka riga suka jona mata , Bai dube su ba kamar yadda bai ce kome ba illa bakin sa da tun-tuni yake motsawa da alamun addu'a yake yiwa ƴar sa , Shi da kan sa ya raba jikinta da duk wasu na'urorin su ba tare da ya ajiye gawar ta ba ya jaa farin mayafin su na asibitin ya rufe fuskarta zuwa jikinta da shi , bayan ya shafe fuskarta da tafin hannun sa . Cigaba yayi da zama a wajen yana riƙe da ita tamkar wanda ya samu ɗaukewar tunani . Ganin haka ya sa likitocin da suka rage su biyu suka fita , Hajja ta ƙarasa wajen su Yakaka tana ba su baki , da har yanzu basu bar kuka ba . Turo ƙofar aka yi Tafeeda ya shigo tare da shi dattijo ne wanda yana sanya ƙafa a ɗakin ƙamshinsa ya gauraye ɗakin da ya sa Youssouf ɗago kansa suka haɗa ido , Maimartaba Sarkin Maraɗi Abdoul-azizou Baskore , ya taka ya ƙarasa gaban gadon da Youssouf yake zaune riƙe da Gawar ƴar sa , "Youssoufa , Ya ƙira sunan sa . Ɗago da kansa yayi a karo na biyu , laɓɓan bakin sa na karkarwa da kyar ya fisgo kalmomin da a tun farkon samuwar Mama yake tsoron Furta su ga Maimartaba a tsa-tsan idanun sa , a yau neman tsoron ya yi ya rasa a lokacin da Mama ta ƙare ta zama Babu . " Baaba , ɗiyata ce , wannan Mama ce , ɗiyata ce , ta rasu , Mama ta rasu ta barni Baaba . Kuka ya sake fashewa da shi idanun sa na zubar hawayen da suke ɗiga akan gawar Mama , Maimartaba sai ya zare gilashin idanun sa , da bayyanuwar sabon yanayi akan fuskar sa saɓanin wanda ya shigo da shi , Yayi tsumu ! yana kallon Youssouf da yake cigaba da kuka marar sauti , zuciyarsa ce ta rau-rawa saboda dalilai biyu da suka haɗe mar a lokaci guda . a hankali ya kai hannu ya dafa ƙafaɗar Youssouf ɗin, cike da tausasawa a muryar sa mai ƙwarjini yace , "Youssoufa kayi haƙuri dukkanin mai rai Mamaci yake , Rayukan mu kuma ababen aro ne a gare mu da babu shakka masu komawa ne ga Ubangijin da ya bamu aron su a domin mu bauta masa , Ka dogara ga Ubangiji da zuciya ɗaya, kada ka dogara ga abin da kake tsammani ka sani , a cikin dukan abin da kake yi, ka tuna da Ubangiji, shi kuma zai nuna maka hanyar da yake daidai , Sam, kada ka yarda ka ɗauki kanka kai mai hikima ne fiye da yadda kake, kai dai ka ji tsoron Ubangiji, ka rabu da aikata saɓo , Idan ka kiyaye wannan, zai zamar maka kamar magani mai kyau, ya warkar da raunukanka, ya kuma sawwaƙe maka azabar da kake ciki , "Miƙata ga Tafeeda ka taso mu tafi ga yi mata sutura zuwa miƙata ga kabarinta ,Allah ya jiƙanta , Allah shi sa ta zama dalilin samun afouwar Ubangiji a gareka  . Kalaman Maimartaba sunyi tasiri ga duhuntatciyar zuciyar sa mai ciwo , dan haka sai ya sasssuta riƙon da yayi wa gawar Mama , ya miƙata ga Tafeeda zuciyar sa na tuno masa rana ta farko da ya fara karɓar ta da tafukansa , ya rungumeta a ƙirjinsa ,  sai ga shi a yau ya zareta daga jikinsa da hannunsa ,  zarewa irin ta har Abada , ji yayi tamkar bazai iya ba , tamkar wani sashi na ransa ne ya bar jikinsa . A hankali Tafeeda ya samu damar zareta daga jikinsa , wanda shima tasa zuciyar tayi laushi tausayin Youssouf ɗin ya cika zuciyar sa tare da ƙarin tsoron Allah , da ya tuna irin ƙauna da tsantsar son da Youssouf yake yiwa wannan ɗiyar , da har ta kai ya zaɓe ta bisa ga kowa da kome nashi , duk a domin ya rayu tare da ita ., Sai ga shi domin Ubangiji ya yi masa babbar jarabawa sai ya sanya mutuwa ta raba tsakanin su , a kuma lokacin da kome ya rinchaɓe masa a dalilinta , lalle wannan jarabawa ce maigirma , Mayafin da aka rufe mata fuska da shi ya buɗe lokacin da yake ɗaga ta , Maimartaba ya dubi fuskarta da tsantsar tausayi cike a ransa , "Ubangiji yasa ki zamto dagga ƴa'ƴan da zasu zam silar samun afouwar Allah ga iyayen su daga tarin zunuba su , "Amin Amin Amin, Hajja ta amsa tana sharar ƙwalla , duba guda Maimartaba yayi musu ita da su Yakaka yayi wucewar sa , Tafeeda ya bi bayansa da gawar Mama , Youssouf ma ya sauƙa ya nufi ƙofar ficewa , ya zo ficewa ya waiga garesu da har lokacin suke ƙasa dirshen a zube , muryarsa a ciki yace "ku tasso mu tai ku wanke ta , Shiru suka yi babu wacce ta amsa masa , Ganin ya fita yasa Hajja cewa , "ku tashi mu tafi Falmata , Yakaka kuyi haƙuri kun ji , haka Allah yake ikonsa uwa ta haifo ɗan da ta fi nisan kwana, kuyi haƙuri kuyi ta addu'a mutuwar Mama hutu ce a gareta , kuyi haƙuri . Zuciyoyin su a lokacin basa aikin da ya wuce na kuka da jin raɗaɗin mutuwar ƴar da suka shirya sadauƙarwa a domin ta sai gashi mutuwa ta ɗauketa a lokacin da kowaccen su take jin rayuwarta kachokam zata sadauƙar domin ta tsaya tare da ita , Suka miƙe ƙafafun su babu ƙarfi suka rufa masa baya , a motar da suka zo a ciki suka koma sai dai wannan karon wani ne ke jaan motar da basu kai ga sanin sa ba , Gidan suka tarar da yalwar mutane da suka wuce yadda suka barsu a farko yawa , Mutane maza da suke sanye da kaya mai launi guda , da kuma mata a falon nasu , Yakaka da Falmata ratsawa suka yi basu dubi kowa ba suka wuce ɗakin da yake na Falmata , suna shiga su duka biyun kuka suka sake sawa , a tsakanin su an rasa mai rarrashin wani , Shigowar Tafeeda ɗauke da gawar Mama shi ya dakatar da ƴan guna-gunin da ya fara tashi bayan wucewar su Kai tsaye ya miƙata ga Hajja wacce take raƙube daga gefe tunda ta shigo babu wanda ya dubeta bare su amsa gaisuwar ta'aziyyar da take yi musu da basu kai ga sanin wa ya rasu ba , ganin sun yi biris da ita ya sa tayi shiru tana sharar ƙwallar ta , "Ki miƙata ga uwayenta sui mata wanka , su shirya ta yanzou za'a kawo likkafani , Sai ta ƙarbeta ta ratsa ta tsakanin su ta wuce ɗakin Falmata , zuwa lokacin hankalunsu baki ɗaya ya koma ga Tafeeda , Bai jira sun tambayeshi ba , ya ce  "Diyar Biyamuradi Youssoufa ce da Allah ya amshi ranta a yanzou , Daga haka bai ɗora kome ba ya juya ya fita , Shiru wajen ya ɗauka , kafin lokacin da Hamshaƙiyar matar da ita ce ƙwal ɗaya a bisa kujera ta motsa , fuskar ta da wani yanayi da kai tsaye ba'a iya fassara shi ba ta soma da cewa , "Allahu Akbar innalillahi wa inna ilaihi raji'oon , kaico yarinya wahalar ki ta ƙare kin kuma huttashe da wasu dagga samuwar baƙin-ciki sanadin duban ki , to Allah shi jiƙan ki , ta tabbata dai Youssoufa yana da ɗiya mai shekarun ya wannan da kuma Amre ko ba Amre ? Bata tsaya ba ta cigaba da cewa , "Mutumin da ya ƙi faɗar gaskiya yana haddasa wahala, wautace babba a ɓatar da lokaci akan aikin banza , mutumin da ya ƙamnaci zunubi ya irin haka , ai ya shiryawa hukunci ne , zunubi da kunyata kuwa tare suke rungumar mai su, shiyasa asharari bashi da wata ƙima  , Ta murza zoben hannunta , tana wani ɗan guntun murmushin cikar buri , ta  ɗora " gaskiya ita dawwamammiya ce ƙarya kuwa ai ƙurarriya ce , ɗan da ya jawo wa Mahaifinsa ɓacin rai ya haka ,? Ai abun baƙin-ciki yake ga Mahaifiyarsa , to wanne farin-ciki za'a yi da samuwar baragurbi cikin 'ya'ya ? A hankali Adda Ammi ta ɗaga kai ta kai ganin ta gareta bayan gama jawabinta lokacin da ƙaramar jakadiya tace , " Babu shakka ko kokonto cikin kalamanki ranki ya daɗe , kowa ya aikata abunda ransa ke so zai ga abunda bai so a lokacin da bai so ba , Kallon-kallo aka yi tsakani Ammi da Ubbo da kawo yanzu suka rasa halin da zuciyoyin su ke ciki kan mutuwar ƴar ɗan uwansu da ake duk wani ƙiƙi-ƙaƙa akanta , Sai dai kalaman Matar da take mazaunin uwa agare su , Matar Mahaifinsu , da kuma ta wakilci Mahaifiyar su wajen wanzuwarta anan , da kalaman nata ke nuni ƙarara da tazorci gami da kausasawa ga ƙaninsu , ko kusa bai musu daɗi ba , duba da cewa wajen gauraye yake da bayun su ,waɗanda Youssouf shugaba yake a wajen su duk da laifin sa , sai dai su basu da ikon tankawa ,"Hajiya Mama uwa take kuma shugaba a gurin su  Ba'a ɗau lokaci ba Tafeeda ya dawo hannunsa riƙe da likkafani , ya miƙawa Ubbo ba tare da yace kome ba , Sai ta karɓa ta nufi ɗakin da ta ga sun shiga ta tarar da su su ukun suna kewaye da gawar Mama da take shimfiɗe a ƙasa , Yanayin da ta gansu ya taɓa ranta , bata ce ƙala ba ta miƙawa Hajja likkafanin , Ta juya , har ta kai ƙofa ta juyo , "kun iya wankan ? Ta tambayesu Babu jinkiri Yakaka ta gyaɗa kanta , sai ta juya tayi ficewarta tana ɗauke ganinta daga kan hoton Mama da yake bangon ɗakin Falmata , tsananin kamannin da yake tsakanin Mama da nata ƴa'ƴan ya girgiza ranta . Yakaka ita ta wanki gawar Mama da take rungume a jikin Falmata , ƙwarar idanun su bata huta ba wajen zubar hawaye , Tunawa Yakaka take tun daga ranar da suka ɗora ƙazamtatciyar alaƙa da Youssouf , har zuwa ɗaukar rainon cikin ta da ta samun ta ta haramtatciyar hanya , zuwa da ranar da ta haifeta , da ko fuskarta bata kai ga gani ba , ta tuno da ranar da ta zo irin kallon da tayi mata dake bayyana tsoro da rashin sanayya , ' tsawon rayuwar da Mama tayi shekaru shida a duniya bazata ɗorar da kome na daga rayuwar yarinyar ba , ƴar da ta ƙi kallonta lokacin farko da ta fito duniya , ta kuma tafi ta barta bata ji tausayin ta tayi tunanin me zata ci ta rayu alhalin abincinta na jikinta ba , ina zata ji ɗumin jikin uwa irin wanda jariri ke buƙata a lokaci na hunturu ? Babu shakka Samy Baby ta zalunceta da ta cisgeta daga cikin ƴar gajeriyar rayuwar ƴarta , ta yi mata yaudara mafi girma da ciwo , irin ciwon da ba zai rabu da ruhinta ba har ta koma ga Maliccinta , " Mama Allah ya jiƙan ki yasa kin samu hutu dawwamamme daga barin rayuwarki mai cike da jinyar gangar jiki , ki yafe min Mama , ki yafe min , addu'o'i ta cigaba da yi mata tana wanke ta . Bayan sun shiryata suka fito da ita , Hajja ta fita ta ƙira Ubbo , zama tayi a ɗakin sannan ta ƙira Tafeeda ta sanar da shi an shiryata ,  babu jimawa suka shigo su biyu da wani , suka ɗau gawar Mama zuwa waje da za'a sallaceta , Falmata kasa riƙe kukan da yazo mata tayi ta fashe da kuka mai ƙarfin gaske , dake bayyana jin ciwon rabuwarta da ƴar da ta ƙwallafawa rai fiye da abunda ke cikin cikinta , Ƴar da ta so tare da sadauƙar da kome a domin ta , ƙaunar da ta mata ta fara daga ranar da ta rungumeta a jikinta bayan rashin mahaifiya da tayi , ta ɗau alwashin maye mata gurbin uwa da ta rasa , ta dunga tuno da yadda suka ƙaunaci juna ita da Mama , da bata san tana da wata uwa ba bayanta har ta koma ga mahaliccinta ita ce mahaifiyarta ɗaya tal, tabbas Mama ta bar mata gurbi a zucia sa babu ranar cikata shi . *** Tamkar wutar daji haka labarin mutuwar ɗiyar Biyamuradi Youssouf/MaJor Youssouf da mutane basu san da wanzuwarta ba ya dunga kewaya ko'ina ɗauke da mummunan tambarin da Youssouf ya ƙi tabbatuwar sa ga rayuwar Mama sai ga shi bayan mutuwar ta labari ya bayyana an kuma ƙira ta da sunan da bai so ba . Zaman makoki sosai ya kankama tun yammacin ranar da aka bizneta da kuma tun bayan jana'izar da Maimartaba sarkin Maraɗi da kansa yayi limanci , ya bar wajen tun kafin dawowar su daga maƙabarta , Ƙarƙashin rakiyar maƙarrabansa da suka zo tare suka koma , waɗanda mafi yawa manyan fada ne , masu faɗa a ji a harkar sarautar masarautarsu da amintattun manyan bayunsa , zaɓaɓɓu da aka aminta da Amanarsu Da tafiyar tasu musamman ta samo asali ne kan zuwa su ganewa idanunsu inda Youssouf ɗin ya ɓoye yana rayuwar banza kamar yadda aka yi ta jita-jita a kwanaki zancen kuma ya dawo kunnuwansu Amma suka yi binciƙe basu samu shaida ba ko guda a wancen lokacin Sai fa da yanzu shaida ta bayyana ta hannun Mouhammadou da yace shi ma fa bayani aka ba shi , Mafiya yawan masu zuwa ta'aziyyar abokan aikinsa ne da matan su sai kuma tsirarun mutanen gari da yake mutunci da su , daga masarautar su babu mutum guda da ya ƙiraye shi ko kuwa ya zo yi masa ta'aziyya tun bayan juyawar tawagar sarki da kuma ta su Hajiya mama , Tsakanin Hajiya Umma ko matansa babu wacce ta ƙira shi , haka ma 'ƴan uwansa idan aka cire Ubbo da Ammi da kawo yau da ake kwanaki biyu da mutuwar Kullum suna zuwa gidan nashi su yini a karɓi gaisuwa da su duk a ƙoƙarin su na son ganin sun rufa asirin ɗan uwansu daga mutanen da basu riga da sun san ta hanyar da ya samar da Mama ba , Sai dai a yau su ma sun kudurce cewa sun yi zuwan ƙarshe dan haka suka yanke shawarar yi masa magana , Har falon sa suka shiga suka tarar da shi , tare da Tafeeda da tunda aka yi mutuwar yana tare da shi , duk da cewa babu wata doguwar mu'amala ko da kuwa ta maganar baki ce da take shiga tsakanin su , A zaune suka tarar da su shiru tamkar kurame , shi Tafeeda yana aikin latse-latsen waya shi kuma Youssouf yayi tsumu irin yanayin da yake ciki tun bayan mutuwar Mama , Babu karsashi suka gaisa , bayanan suka yi shiru ,suna nazarinsa da ya sunkui da kansa , baki ɗaya yayi wani irin sanyi har ƴar rama yayi , ba kaɗan ba mutuwar ƴar sa ya taɓa rayuwar sa , Cikin taushin Harshe Ammi ta fara masa nasiha kan laifinsa na aikata zina da ta kai shi ga haihuwar Mama , har zuwa yin aure ba tare da sanin iyayensa ba , bayan haka ta tambaye shi tsakanin Yakaka da Falmata waye uwar Mama ? Nan ya basu amsa da cewa Yakaka ce mahaifiyar ta , Ta tambayeshi kuma ta yaya yake auren Falmata alhai ƙanwace ga Yakaka kuma suna tare guri guda ?    Nan ya basu labari a taƙaice kan yadda aka yi ya auri Falmata da zaton cewa Yakaka ta mutu ne , sai kuma kwanakin da suka dawo daga USA ya ganta a gidan bashi da wani masaniya kan labarin da ya shafe ta .   Duk shiru suka yi , kafin ubbo tace " to tunda Allah ya gwada karshen kome da ya zare wannan ɗiya a tsakani domin kawo maslaha a gare ka, sai kayi ƙoƙarin gyara duk wasu kuskuren ka , "tunda daman domin riƙon ita ɗiyar kake amren innar ta ai sai yanzou ka sau amren su yi tafiyar su , kai ma ka koma ga iyayenka ka biɗi afouwarsu , su yafe ma sabadda rayuwa tayi maka kyau Youssoufa , ka fuskanci aikin ka cigaban rayuwarka ka ji kou ? Ba tare da ya ɗago kan sa ba yace " to naji , Kallon rashin gamsuwa da amsar sa suka bi shi da shi , amma basu jaa zancen da tsawo ba suka rabu da shi , saboda sun san muddin ya tafi Maradi sai ya saki auren Falmata ba zai yiwu ya bijirewa iyayensa ba bayan tarin laifin da yayi masu muni . Basu bi ta kan su Falmata ba bare su yi musu Sallama suka fita a gidan cikin motar Tafeeda , suka bar Youssouf shi ɗaya tal a ƙofar gidan , Matsawa gefe yayi ya samu waje ya tsugunna , kewar ɗiyar sa tare da ciwon rashin ta suna taso masa , kwanakin da suka biyo bayan mutuwar ta basu zo masa da sauƘi ba sanin da yayi bata raye a duniya yana murƙushe duk wani kuzarinsa , baya iya bacci daga ya rufe ido fuskarta ke yi masa gizo muryarta na amsa kuwwa a kunnuwansa , baya son doguwar magana da zata katange shi daga yin addu'o'i  , ko abinci sai yunwa ta kai masa maƙura yake iya tsakura ya ci . Ƙaunar Mama dabance a wajen sa ko cikin abubuwan da yafi so a duniya tana a sahun farko , yasan a cikin 'ya'ya ba zai samu ya ita ba a samun zallar so da ƙauna daga wajen sa tayi zarra , sai ga shi tafiya bata miƙa ba , mutuwa ta shafe tsakanin su , ta ɗauke masa sanyin idaniyar sa . 'yar da silar ta ya haɗu da Fatima zahra har tayi sanadin ƙulluwar aure a tsakanin su ta wanzu tsawon lokaci tana ƙulla kusanci a tsakanin su  , har sai da ta sa bai farga ba ya faɗa tsundum cikin ƙaunar innar ta , Tunanin Falmata ya zo masa , a tun ranar mutuwar Mama rabon da ya sanyata a ido ko ya ji muryar ta , ya san tana cikin halin ɗimuwa kwatankwacin wanda yake ciki tana kuma buƙatar lallashinsa ,  Sai dai ba shi da wani sauran dauriyar sake fuskantar wani tashin hankalin da zai iya tasowa daga gareta bayan sanin da tayi cewa shi da Yakaka sun rufeta akan alaƙarsu da haihuwar Mama , bashi da tabbaci kan yadda ta ɗau lamarin , Dan haka ya zaɓi ya bata iska , Kafin zuciyar sa ta gama yanke shawara kan hukuncin da yake son zartaswa a gobe . *** Yakaka da Falmata sun yi kwanaki biyun cike da kewa da jin ciwo na rashin Mama , Koyaushe su na ƙule a ɗaki , basa fitowa falo wajen da su Ubbo suke bare su ga juna , Hajja ita ke kai kawon kula da lamuran gidan, ko abinci kai musu take har ɗaki , duk kuwa da cewa basa yi masa wani cin kirki , Wani irin zaman shiru suke yi marar armashi da tunda suke su biyu irin shirun mai kama da na tsakanin baƙi juna bai taɓa gifta tsakanin su ba , kowacce tana jinyar ruhinta Yau bayan sun idar da Sallar Azahar, suna bisa sallayun su , Falmata ta dubi sashin da Yakaka take , ta ƙira sunanta a hankali , " Yakaka , Yakaka ta ɗago kan ta ,daga karatun da take yi , ta amsa ƙiran da tayi mata tare da tasowa ta dawo kusa da ita ta zauna ta riƙo hannun ta da irin kulawar da ta saba bata tun tasowar su , Falmata ta ƙure kallonta ga Fuskar Yakaka da take iya hango haskenta , tace "Yakaka , ki faɗa min , ki bani labarin tsakanin ku ,    Tayi shiru kaɗan , "ki bani labarin na gaskiya tsakanin ku da Baban Mama , kuma ki bani labarin rayuwar da kika ki bayan haihuwar Mama Alhalin bakya tare da mu ? Ki bani labarin gaskiya Yakaka . Shiru Yakaka tayi cike da zullumi sai dai ta san abune da tasan da faruwar sa ,tun gabannin ta tambaye ta dan haka ya zama dole ta sanar da ita dukkanin wata gaskiya da ta nemi da ta sani , Muryar ta babu kuzari ta fara bata labarin tun daga Rana ta farkon haɗuwar su da Youssouf , har zuwa ranar rabuwar su ta ƙarshe , ta ɗora da cigaba da sanar da ita irin gadar zaren da Samy Baby ta haɗa mata tun kafin zuwan ranar haihuwar Mama da a ƙarshe tayi nasara ƙarƙashin jagorancinta da mummunar huɗubar ta tayi tasirin rabata da rayuwarsu ita da Mama 'yan mintoci kaɗan bayan haihuwar ta , dakatawa tayi tana jin tashin hankalin yadda Falmata ta zare hannunwanta dake cikin nata , ta ɗago kai tana kai kallon ta ga fuskar ta ganin yadda hawaye suke zuba daga gurbin idanun Falmata ya ruɗa ta , Sai dai bata da wani zaɓi illa cigaba da sanar da ita gaskiyar kome kamar yadda ta alƙawarta , bata tsahirta ba ssi da ta gama tas da bata labarin rayuwarta a garin Abuja gidan samy baby , taimakon da Malama Maryam da ƴar ta Lubna suka yi a rayuwarta ,  har zuwa komawarta gida Maiduguri wajen Prof . Ta ɗago kanta tana nazarin Fuskar Falmata wacce tayi ƙasa da idanunta ya zuwa yanzu ta daina hawaye ,  riƙe hannunta ta sake yi muryarta na rawa ta cigaba da cewa " Falmata na san ni mai laifi ce a wajen ki , amma dan Allah kiyi haƙuri ki yafe min , nayi kome ne gurin ƙoƙarin na baku rayuwa mai kyau bansan cewa ace na kama hanya ne na rusa mana rayuwa ba , ki yafe min ki zo mu koma Nigeria wajen Baba prof shine kaɗai mutumin da ba zai kore mu ba , ki rabu da Rayuwa da Youssouf kamar yadda Mama ta bar mu , shi ɗin ba kowa bane da ya wuce Maƙaryaci Mayaudari da ...... Miƙewar da Falmata tayi ita ta hana Yakaka ƙarasa zancenta , da kallo ta bi ta lokacin da ta nufi ƙofar banɗaki ta tura ta shiga ta rufo ƙofar ba tare da ta waiga gareta ba , zama tayi cikin wani irin yanayi mai cike da rashin madafa , nadama na sake lulluɓar ta , ko Falmata bata buɗe baki tace mata kome ba ta fahimci tana fushi da ita , fushi kuwa mai tsanani , da ya sa taji tsoron sake yin wani yunƙuri domin tana gudun faruwar wani abu marar daɗi a tsakanin su , Fiye da minti talatin ta kwashe a zaune tana jiran fitowar Falmata daga banɗakin da tunda ta shiga bata jiyo motsinta ba , har ta fara tsorata tana tunanin tashi ta ƙira ta , sai ta ga ta murɗo ƙofar ta fito , daga fuskarta har tufafin jikinta a jiƙe suke , sai tayi kasaƙe tana bin ta da kallon tsoro , ganin yadda idanunta suka kumbura alamun kuka tayi mai tarin yawa , Kayan jikinta ta sauya ta zo ta janye sallayarta da take gaban Yakaka ta matsa gefe guda ta fara sallah , Gaɓɓan jikinta baki ɗaya sun daɗa sanyi Shirun Falmata kuma ya sa ta ɗeɓe tsammani , cikin zuciyarta sai ta fara tunanin mafita , Ta shiga bijiro mata da kome da ya wakana daki-daki tsakanin da Youssouf wanda tuni ta fahimci kason nata laifin yana neman zarta na Youssouf tun a farkon fari , ai ita ta fara bada kanta cikin salama , sannan ta cigaba da zama rakuma da akala wajen biye masa aikata zunubi , mafi girman laifin da ta aikata shine gudu da tayi ta ƙyale Mama da Falmata , wanda ta nan Youssouf ai ya fita amfanarwa ga Rayuwar Mama da ya haɗa su da ita da Falmata ya tallafa har ma ya zamto sanadin samun lafiyar idanun ta wanda tun akan hanyar su ta zuwa Niger Hajja ta sanar da ita samun lafiyar idanun Falmata , ranta kuma ya cika da farin-cikin da ta ƙi nuna shi a fili saboda kada ta nuna yabawa ga Youssouf bayan tarin laifin da take tuhumar sa da shi da kuma ƙudirin da take tafe da shi na son raba zaman su , Sai dai a yanzu da irin yanayin da Falmata ta nuna bata hango alamun zata samun haɗin kanta cikin sauƙi ba , ita kuwa ai bata da sauran ƙarfin zuciya , mutuwar Mama ta kwace mata duk wani karsashi nata , Jin an ƙira sallah ya sa ta miƙewa ta ɗaura Alwala ita ma ta tada sallar la'asar , Bayan sun idar gani tayi Falmata ta miƙe ta hau gadonta ta kwanta tare da jaan bargo har kai ta rufu , duk kuwa da cewa garin babu sanyi , Jugum tayi tana hangenta , kafin ta ce Falmata , garin ai babu sanyi meyasa kika rufu haka ? Biris tayi da ita bata amsa ba , jikinta sai ya sake yin sanyin sanin da tayi cewa Falmatan tana jin ta sarai ƙin tankawa tayi , Sai ta miƙe ta naɗe sallayar , takunta ba ƙarfi ta fita ta ja mata ƙofar ɗakin bata yi taku uku ba ta ji ƙarar sanyawa ƙofar makulli da Falmata tayi , Sai ta waigo tana kallon ƙofar , tayi murmushi mai bayyana ciwon da zuciya ke yi , hawaye na taruwa a gurbin idanunta ƙwarai abunda ta fuskanta daga Falmata a yau ya taɓa ran ta , ɗakin Hajja ta koma bata sake bin ɗakin Falmata ba . Daren ranar babu wanda ya ci abincin dare a tsakanin su Ukun Youssouf , Yakaka ,da kuma Falmata haka kowannen su ya kwana yana saƙa abunda yake ganin zai fissheshi , Ƙarfe huɗu da rabi da Hajja ta farka ta tarar Yakaka ta haɗa kayanta kaf , cikin ƴar jakar da ta zo da shi da tana zaune shiru ta jingina kanta da jikin bango , Tausayinta ya kama Hajja , bayan ta ɗaura Alwala ta fito sai ta zauna a gefenta , "Yakaka uwar Mama Ta ƙira sunanta , bata amsa ba amma ta maida hankalinta gareta , " Ya naga kin ɗauko jakar kaya haka ?ko.. " Tafiya zan yi Hajja , yau zan koma Nigeria , daman domin na gansu na zo kuma ai na gansu , na ga mutuwar Mama a idanuna , babu sauran zama da zan sake yi zan tafi yau . Ta ƙarasa zancen hawaye masu ɗumin gaske suna sauƙa daga idanunta Kamo hannun ta Hajja tayi , muryar ta a tausashe tace " kiyi haƙuri Yakaka dukkanin abunda kika ga ya faru ga Rayuwar Bawa tun gabannin a halicce sa yake a rubuce cikin kaddarar rayuwar sa ,  kar ki bari shaidan ya raba tsakanin zumuncin ku ke da ƴar uwar ki , kan abunda ya gabata ku duka uku kaddarar rayuwar ku ce ta zo a haka , ke kece Babba ki riƙe zumuncin ku ƙam kar ki bari kowanne mahaluƙi ya shiga tsakanin ku , ku biyu ne rak a duniya ko kuwa kuna da wanda ya wuce junan ku ne ?? Girgiza kai Yakaka tayi alamun a ah , sai kuma tace " Hajja Amma Falmata ta samu wanda ya fini tu..... " kul kar ki bari zuciyarki ta miki mummunar saƙar da zata wargaza muku zumuncin ku , kiyi haƙuri ki maida kome ba kome ba , kiyi haƙuri da jarabawar Ubangiji Allah zai miki tukuici da mafificin abunda duk kika rasa kin ji ko ? " to Ta amsa tana share hawayenta , Hajja ta cigaba da cewa , "yadda kuka haɗu kuna murnar ganin juna kar ku rabu kuna zargin juna ku rabu da farin-cikin da zai ƙara danƙon zumuncin ku kin ji ko ? " naji nagode Hajja , Shiru suka yi suna saurara lokacin da suka ji an taɓa ƙofar falon , sai dai basu kawo kome a rai ba ga zaton dukkanin su Falmata ce ta dawo daga turakar Mijinta , Hajja ta ɗora da cigaba da yiwa Yakaka nasiha tare da gwada mata girman zumunci. Da ya sa ta jin sabuwar ƙaunar 'yar uwarta na game mata jini , Lokacin da gari yayi shaa , sai ta fito falo da jakar kayanta tana jiran fitowar Falmata domin suyi sallama ta kuma sake neman yafiyarta , 'yan kuɗaɗenta kimsnin dubu goma sha uku a ƙulle a marar ta , sai ta ware dubu uku da ɗari hudu zata bawa Falmata kyautar su ita kuma ta san dubu goma zai sada ta da birnin Maiduguri har ƙwaryar gidan Prof . Zaman fiye da mintoci goma ta yi lokacin da ta ji an shigo Falon a hankali ta kai ganinta kan sa yana shirye tsaf cikin kakinsa na soji , sai ta tuno da ganin da tayi masa a baya can , Da sauri ta ɗauke kanta ta mayar da ganinta ƙofar ɗakin Falmata , Shima a ɗarare ya ƙaraso falon fuskarsa babu walwala , a kusan tare suka furta kalmomin "ina kwana ? Shi ya riga ta amsawa da "lafiya , Sai duk suka yi shiru , shi bakinsa ɗauke yake da jawabi duk da cewa a yau ya hango sassauci daga gareta a karon farko , Ƙarasowar Hajja wajen ya sa shi zama akan kujerar da take kusa da shi , gaisawa suka yi tana sake yi musu ta'aziya su duka biyun , har ta miƙe sai yace "Hajja ina Fatima ? Hajja tace tana ciki Babban soja , a ƙirata ne ? "eh Hajja a ƙirata , Hajja ta nufi ɗakin Falmata , Haka kawai Yakaka ta ji zuciyarta ta tsinke , a karo na farko ta ji tsoron kar Youssouf ya furta cewa ya saki Falmata da tun-tuni ta fahimci ta faɗawa son shi , tausayi take ji , ita ta san yadda raɗaɗin so yake , bata fatan Falmata ta ɗan-ɗana zogin rasa masoyi , a yanzu zata so Falmata ta tsira da masoyinta , abunda ke cikinta kuma ya rayu kusa da mahaifinsa ƙarƙashin gatan uwa da uba a lokaci guda , Dan haka ta yunƙuro da zummar yin magana ta shaida janyewar ƙudirinta akan sa , fitowar Hajja ya katse ta , inda take sanar da su Falmata bata ɗakin , "tana ina Hajja ? Youssouf ya tambaya da ɗan shakku a muryar sa , "ban sani ba Babban soja kuma bata can sashin naka ? Ya miƙe tsaye lokacin da yake cewa "bata can ai Fatima batta je ga sashi na ba , su dukkanin su sai suka yi tsaye cikin ɗarsuwar sabon tashin hankali a rayukan su Kamar haɗin baki sai suka bazama neman ta , lungu da saƙo na gidan , Youssouf da Yakaka suna haɗawa da ƙwalla ƙiran sunanta , amma ko alamu babu kurwar ta a gidan , dawowa suka yi suka haɗu a falon zuwa lokacin Yakaka kuka take yi , shi kuwa Youssouf idanunsa ne suka kaɗa jawur ,  da wani irin tasowar mummunan ɓacin rai lokacin da tunanin sa ya gama hasaso masa abunda ke faruwa ya dubi Yakaka da wani irin sauti yace " Ina kika kai ta ? Ina kika ɓoye min Matata ?  Kiyi gaugawar sanar da ni kafin ki riski fushina Yakaka .. Yakaka ta zaro ido da maɗaukakin mamaki tana kallon sa , "ita Youssouf yake nufin ta sace Falmata ƙanwarta ? Wanne irin mummunar kalma ne wannan yake jifatan ta da su ??    Saɓon ɓacin rai ya bijiro mata . Assalamu Alaikum masu karatu dafatan kuna lafiya ? Wannan shafin kachokam ɗinsa sadauƙarwa ne ga duk wasu iyayen masu ɗauke da cutar Amosanin jini ,( Sickle Cell Disease) Ku sani ya ƴan uwa Allah ya ɗora mana ne domin ya san zamu iya , wataƙila kuma domin hakan ya zamto hanyar samun Rahamar Ubangiji a  gare mu mu iyayen da kuma su da suke ɗauke da cutar ( muna fatan haka ) Ku sani cewa cuta irin wannan mai wahalarwa baiwa ce da ba kowa Allah ke ɗorawa ba , dan haka muyi ƙoƙari wajen basu kulawa tare da haƙuri domin cinye jarabawar da Allah ya yi muna ta dalilinsu . Kada mu danƙwafar da su , kada kuma mu banbanta su da sauran ƴan uwansu masu lafiya , ƙarfafawar mu tamkar ƙara musu lafiya da walwala take yi a gare su, saɓanin haka zai iya sawa suyi rauni su ji tamkar su basu da amfani a lokaci guda su ji sun gaji da duniya . Cuta bata nuni izuwa ga mutuwa kamar yadda lafiya bata nufin tsawitar rayuwa ( nisan Kwana )  fatan mu Allah shi iyar muna , ya yi mana maganin abunda ya gagare mu , ya wadace mu da lafiya mai amfani . Ina miƙa ta'aziyya ga dukkanin iyaye ,kakanni 'ƴan uwa na waɗanda suka rasa rayukan nasu ta sanadin ciwon Amosanin jini Sickle Cell Disease . Jinjinar kuma ta tafi gare ku gawurtattun mayakan da Allah ya ratayawa cuta mai wahalarwa,  Da ku nake ( sickle cell Warriors ) ku din ai JARUMAI ne da suka banbanta da saura , ku cigaba da nuna jarumta watarana akwai waraka zata zo inshaAllah . Nagode . [12/10/2019, 2:44 PM] +234 706 503 6187: MAFARI ( Hargitsin Rayuwa) Umm'muaz 44 Cikin motar ƙirar Golf 2 Wagon da take shilla gudu akan titin da zai sadu da jahar Tahoua . Falmata ce a zaune daga kujerar da take daura da Direban da bakinsa yake cike da goro ,  yana ta bin wakar Sa'adu bori mai taken 'soyayya abun yi ce ,da take tashi ta cikin sifikun motar kamar zai fasa mata dodon kunne ,  ta  kare fiye da rabin fuskarta da ɗankwalin doguwar rigar jikinta da ta sanya hijabi a madadin sa Ita ɗaya ce ƙwal mace a cikin motar sauran mazauna gidan baya na motar duk maza ne matasa majiya ƙarfi *** Lokacin da ta samu isa tashar mota na birnin Niamey da misalin ƙarfe biyar da rabi na asubahi , babu yawaitar mutane a tashar da kyar ta samu wani dattijon ɗan kamasho inda ta shida masa Maidugurin Jahar Bornon Nigeria take son zuwa , A mamakance dattijon yake kallon ta , kafin yace mata , "kai tsaye Borno zaki tai dagga nan yarinya ?ko dai Sokoton Nigeria zaki tai dagga nan , a can kuma ki tai Borno ? "Maiduguri zan tafi daga nan Baba, dan Allah ka kaini motar da zata tafi can . ta bashi amsa tana share ƙwallar da taƙi tsayawa a idanunta , Da sauri ya tare ta da cewa , "a ah yarinya batun ba na kuka bane kin ga itta motar Borno dagga nan ai wahala take batta samuwa haka a sauƙaƙe , sabadda Borno daga nan tahiya ce miƙaƙaƙƙa ya ta mai yada shege , sai kin tai zouwa zender dagga nan ki shiga ta diffa kafin ki tsallaka boda ki shiga yankin Mobar ta jahar Bornon Nigeria , anya yarinya kina mace budurwa ɗanya shakaf kya iya wagga tahiya ta mazaje ? " zan iya Baba , Allah zan iya , zan tafi ga taimaka min . Tace , zuciyarta na sake haƙaƙewa kan tafiyar ita ce kaɗai mafita a gareta , " to babu laifi , bara shi malam Amadou gayu ya isso domin shi ɗai yake wannan dagon zagon Allah sa dai ƴan tangaran basu riga sun kama kujerun motar ba , dawo dagga nan ki zauna , nan ba da jimawa ba ike isowa , A ɗarare ta zauna akan wani ɗan dandamali ba dan ranta ya so ba domin a matse take ƙwarai da ta bar yankin , Zaman mintoci goma kawai tayi sai ga motar Ahmadou gayu , wata wankakkiyar golf wagon ce da ta ci uban dilken da ake yiwa tsoffin motocin da ake son tada musu da komaɗa tare da ɓoye musu tsufan su . Tayi zaton za ta ga wani matashin saurayi jin ana masa inkiya da "gayu , sai ta ga wani dattijon da ya tasamma shekaru sittin amma ya ƙi sarewa daga yin gayu domin kuwa a tsuke yake cikin ƙananun kayan da suka ɗau guga , ya ci zanzaro ,  kan nan nasa da sanƙo ya cinye rabi rabin kuma gashi ne a tare himili guda da aka yiwa shamfo a taje tsaf-tsaf yana sheƙin Mai . Da fitowar sa gurin ya ɗau ƙamshin ƙaƙƙarfan turarensa na 999 for male . Bai jinkirta ba ya fara goge jikin motar da a zahiri babu wani datti sai ƴar ƙura da ba'a rasa ba , Ɗan kamashon nan shi yayi sauri ya samar mata wajen zama domin kuwa , kamar yadda yayi zato har an riga an kama kujeru huɗu na bayan motar ,wajen mutum ɗaya tak ya rage , Dan haka Falmata bata jaa ba lokacin da aka yanka mata adadin kuɗin da zata biya , ta ƙirga kuɗin daga ciki ƴar karamar jakar hannunta da ita ce tal abunda ta riƙa , ta basu ta shiga gaban motar ta zauna . Sauran mutane huɗun da yake daman sun riga sun kama kujerar motar suna zuwa shiga suka yi ba ɓata lokaci .. Ƙarfe shidda cif motar su ta bar cikin tasha ta ɗau hanyar da tafiyar da zata iya kai su kwanaki biyu kafin isar su Yankin jahar Borno Nigeria  . *** Tunda suka kama hanya ta kwantar da kanta jikin gilashin , bayan ta rufe rabin fuskar ta , A zahiri ta ɗora idanun ta ne bisa kan titi da ƙura irin ta juyin yanayin shigowar bazara ke tashi daga kan rairayin hamadan dake gefen titin , Sai dai can cikin tunanin ta ruhi da ƙwaƙwalwarta sun zurfafa ne cikin tsinkayen makomar rayuwarta tare da rarrabe fari da baƙi , Tun a jiya da ta san haƙiƙanin gaskiyar kome take jin tamkar mafarki ne tayi ba ido biyu ba , Tayaya za'a ce Mutane biyu masu girman daraja a rayuwar ta sun yi mata irin wannan mummunan rufa-rufa ? Ashe Baban Mama da ta ɗau duk wani aminci da yarda ta ba shi , ta riƙe shi a matsayin mafi nagarta cikin mutane , shi ɗin mayaudari ne , fasiƙi , yayi zina da yayarta , ya gudu ya bar ta da cikin , tsakanin rayuwa da mutuwa , sannan daga baya ya dawo yayi ƙarya ya aure ta , ? Shiyasa mana yake shiga gigita da ɗimuwa a duk lokacin da tayi yunƙurin sanin irin alaƙar da ta kullu tsakanin sa da Yakaka , ashe Azzalumi ne . Yakaka ta cutar da ita tun farko da bata taɓa sanar da ita irin alaƙar da ta kulla har ta kai ga samar da Mama ba , Ashe son da Yakaka take iƙirarin tana yi mata bai kai nan ba , tunda har ta iya gudu ta bar su ita da Mama jaririya akan ɗa Namiji bata ko tausaya musu ba  , ta tuno irin yadda fitar Yakaka daga rayuwarta ya jiggata mata rayuwa , ta tuna irin halin ƙunci da ciwon rai da tayi fama da shi , ta tuna da cikin kowanne irin yanayi na farin-ciki ko baƙin-ciki a rayuwarta tana yin su ne tare da tarin kewar Yakaka , bata taɓa sabawa ba da rashin ta , bata taɓa daina kukan mutuwar ta ba kamar yadda cikin duk wasu sallolinta bata tashi ba tare da tayi mata addu'ar samun rahamar Ubangiji ba , da yafiyar sa . Amma ashe wai duk tsawon lokacin nan Yakaka tana raye cikin ƙoshin lafiya da kwanciyar hankali bata taɓa waiwayar su ba ?  kuma wai da son ranta ta bar cikin rayuwar su ?  shin wanne irin so ne maigirma haka Yakaka take yiwa Youssouf ? Babu shakka tana iya tuno kaɗan daga cikin soyayyar da Yakaka take yiwa Bature kam silum ɗin ta , Dan haka tun jiya ta riga ta sulluɓe Youssouf daga ran ta , take kuma kankare duk wani ɗiso na ƙaunar sa daga ran ta , tana ƙenƙesawa zuciyarta Youssouf ya haramta a gareta . Tunanin irin cutar da su biyun suka yi ga ɗiyar su Mama yana nuƙurƙusar ran ta tare da ƙara mata baƙin-ciki a duk bayan ƴan daƙiƙoƙi , Cikin ƴar taƙaitatciyar Rayuwar da Mama tayi babu shakka bata yi maraicin uwa ba , ta cikace mata gurbin da Yakaka ta bari ƙarƙashin son zuciyar ta , A ganin ta daga Youssouf har Yakaka bata su dace da zama Iyayen Mama ba , mutuwar Mama kuma hutawarta ne daga shan takaicin gori da aibatawan mutanen duniya , Ta zaɓi da ta tafi ta barsu tare tunda su biyun babu abunda suka sani sai tsananin son zuciyoyinsu , su zauna tare domin su biyun ai sun dace da juna , Ita zata koma Maiduguri , ta roƙi Prof kan ya raba auren su da Youssouf , babu wani sauran zama a tsakanin su tunda wacce ta aure shi a domin ta bata raye a duniyar , Abunda yake cikinta kuma ko Mace ko Namiji nata ne , zata riƙe abunta tayi rainon sa ita kaɗai ko da kuwa zata ɗora kwanon talla ne akanta tayi yawo bakin kasuwanni zata kula da ɗiyanta ba zata taɓa barin ɗan ta yayi maraici ba Alhalin tana raye . *** Duk tafiyarta tsakanin Niger da Nigeria ta yi su ne a halin makanta , ƙarƙashin kulawa da jagorancin Hajja , kuma a motar gida da suke sake babu wata takura , Dan haka bata san kome ba game da hanya , ba gani take ba lokacin da aka yi tafiyar , yanzu kuma da take ganin hanyar dusu-dusu ba zata iya fahimtar cewa an nausa da ita wata hanya ta daban ne saɓanin wacce suka saba bi ba , Tsakanin Niamey da Diffa tafiya ce ta yini da kwana , kusan awanni ishirin , kuma hanyoyin ba sosai suka cika kyau ba musamman idan hanya ta sauƙa ta tsakanin rairayin hamada ,  ga kuma ranar da ta buɗe sosai take bada zafi . Dan haka a wahale sosai take ga kiɗa da ya ƙi yankewa a motar tamkar ɗan wani ƙaramin gidan rawa , waƙoƙi daga na Sa'adu bori , sai na Hajiya Sa'adatu Aliyu "Barmani mai-coge" bayan ƙarar kiɗan ga ta muryar shi kansa Ahmadou gayu da yake bin kowacce waƙa tamkar da shi aka rereta , bakinsa ko gajiya baya yi , Tafiyar su tayi nisa kasancewar Amadou gayu ƙwararren direba ne , azahar tayi musu suna wucewa ta cikin garin maraɗi , Falmata tayi lamo a motar gajiya gami da yunwa da ƙishirwa sun kai ga jiggata ta , babu kome a cikinta sai ruwa da ƙosai da suka saya tun safe a hanya da ba wani cin kirki ta yiwa ƙosan ba . Lokacin da Amaudou gayu ya tsayar da motar sa , a gefen titi kusa da wani wajen sayar da abinci , domin a ci abinci , ayi sallah , daga sama ta tsinci muryar sa , yana cewa , "Maraɗi muke , cibiyar noma da ciyar da Al'umma to ayi harama , ayi sallah a ci abinci ayi kuma gurinsa , idan da mai laruri , ya tai ya sauƙe , domin idan na danna totur , banni dakatawa nan kussa sai mun dangana da Diffa , dan hakka kowa ya ɗau shiri , yauwa . Ji tayi tamkar ta cigaba da zaman ta cikin motar , kar ta taka ƙafar ta a ƙasa domin tunda ya ambaci sunan Maradi tashin hankalin ta ya sake hauhawa , domin idan ba ta manta ba , Maradi shine sunan garin su Youssouf , ita fa a yanzu ƙyamatar duk wani abu da ya shafe shi take yi . ganin idan ta cigaba da zama ita zata kwan ciki , yasa ta yunƙura ta fito , zagayawa ta fara yi neman banɗaki , saboda mararta da take cike . Bayan ta idar da Sallar da tayi akan mayafinta , sai tayi zaune jugum daga inda take tana iya hango kai kawon jama'a ko ta ina a farfajiyar wajen tamkar ƙaramar kasuwa , masu abinci da masu shayi zuwa kan masu sayar da kayan sanyi sune birjik a wajen , Tashin hankalin da take ciki ya hana ta ji wata yunwar kirki tun ranar rasuwar Mama , sai dai tausayin abunda yake cikinta da tasan zai samu ne kaɗai daga abinda ta ci , ya sa ta miƙe ta ƙarasa wajen wata ƴar rumfar sayar da abinci da ta ga mutane na saya sosai , tuwo ta ce a kawo mata miyar yauƙi da kuma kunu bayan ta miƙa kuɗinta ga wata matashiya . Bata san ita kanta a matse take da son cin abincin ba sai da tayi arba da fari sol ɗin tuwon garin shinkafa da miyar kuɓewa busasshiya da aka ɗan ɗiga mata man shanu a ciki , babu laifi abincin su bai cika tsada ba da ɗan aukinsa , domin 'yan madai-daitan curi/mal-mala ne biyu kuma har da nama yanka biyu . Da zaƙuwa ta fara cin abincin bayan ta juya baya daga mutanen da suke wajen , Tas ta cinye tuwon , ta ɗan sha kunun gyaɗa da ɗanyar shinkafa da yake fari sol shima ba'a cika sugar ba . Kamar yadda Ahmadou gayu yace su yi guzuri bayan ta gama cin abincin sau kuma ta sayi gasasshen nama da ruwan roba biyu bata jinkirta ba koma mota , nan ta samu duk kowa ya dawo ita ɗaya ake jira dan haka tana shiga , Gayu ya danna totur suka sake ɗaukar hanya . *** Biyamuradi Youssouf tare da Yakaka da Hajja babu inda basu nemi Falmata ba a tsuƙin unguwar suna haɗawa da cigiya , basu haɗu da ko wanda yace musu ya gan ta ba , Iyakar gigita Yakaka ta shige ta , hawaye da gumin zafin rana sun haɗar mata , tsoronta ɗaya ne kada Falmata ta yanke hukuncin tafiya yawan duniya , kamar yadda ita tayi , ta san halin Falmata sarai , tana da zafin rai idan har aka taɓo ta . Tun a jiyan yadda tayi mata daman ya bata tsoro , sai dai bata yi tunanin zata iya yanke ɗanyen hukunci irin haka ba , meyasa Falmata zata yi mata haka ? Meyasa baza ta yafe mata ba ? Zuwa ƙarfe goma na safe sun gama cire rai da ganin ta , haɗuwa suka yi a falon kowannen su ya yi jugum , Youssouf ya ɗago kansa yana yiwa Yakaka kallon da yafi kama da harara , " Ina sake faɗi miki muddin ke kin ka ɓoye ta , ki fiddo ta kafin na kai ga sani da kaina, A zuciye Yakaka ta katse shi , " Ka daina faɗa min maganar da bata da tushe , Falmata ƙanwa ta ce tare ka gan mu idan har ni ban ce sai ka nemo Falmata ba kai baka isa kace na sace ta ba Dan Allah ka barni na ji da damuwa ta . "Kuyi haƙuri ku duka , lamarin ba na sa'in'sa bane mu ji da tashin hankalin da muke ciki , Babban soja ko za'a kai cigiya kafar watsa labarai ?? Abun yafi kama da sace ta aka yi idan ba haka ba ina Uwarɗakina ta san gari bare har ta fita da kan ta , to ta tafi ina ? Ita da ba lafiyar ido da ta jiki ta cika ba , O Allah gamu gareka , ka iyar muna.     Hajja ta ƙarasa zancen ta tana sake rafka tagumi Tamkar an tsikareta Yakaka ta miƙe tana cewa "muje tasha , tashar da ake hawa motar barin gari , wataƙila Falmata ta tafi Nigeria ne , Cikin ƴan mintoci suka cimma tasha ,  gurin da ake lodin fasinjan zuwa Nigeria suka nufa , suka tarar mafiyawan motoci sun riga sun tafi sai ɗaya ce bata kai ga tafiya ba ita ma mutane biyu ake jira , Babu Falmata a cikin su , dan haka Youssouf ya dunga bin ƴan kamashon yana nuna musu hoton Falmata dake fuskar wayarsa tare da tambayar ko ta hau motar zuwa Nigeria ? Kowa yace bai ganta a tashar ba , zuwa lokacin duk wani firgici da tashin hankali sun zana kansu ɓaro-ɓaro a fuskar sa da tayi jaa , jijiyoyin kansa kuma suka bayyana ruɗu-ruɗu , a sarari ya furta " Fatima ina kin ka tafi ?? Dattijon ɗan kamashon da ya sa Falmata a motar Mallam Ahmadou shine ya ƙaraso gaban Youssouf da yake tsaye riƙe da kunkumin sa , sai duban gabas da yamma yake cikin rashin samun madafa, " ance kun taho ne neman watta ɗiya ko ta tai Nigeria kou ? Cikin sarewa Youssouf ya amsa da "eh , yana share gumin goshin sa , "itta ce wata 'yar baƙa kakkaura mai matsakaicin tsawo tana da zanen barebari a fuskar ta ? Youssouf da Yakaka a tare suka yi rige-rigen amsa masa da cewa "ita ce , tana ina ?    Youssouf ya dora da nuna masa hoton Falmata domin ƙarin tabbatarwa, ya karɓi wayar bayan ya kashe idanu ya ƙure mata kallo , miƙawa Youssouf wayar yayi da yake ta bin sa da kallo cikin zaƙuwa , "Babu shakka itta ce wannan ta zou nan da gefen Alfijir, tana biɗar motar zouwar jahar Borno Nigeria dagga nan kai tsaye , nan nayi mata togaciyar kan nisan dake tsakanin Niame....    "Baba ina take yanzou ? Ta tahi ne ko kuwa tana ina ? A kaikaice dattijon ya dubi Youssouf da ya katse masa hanzari , ya ɓantari goron sa kafin yace   " ta taihi tun motar farko dagga nan kai tsaye zouwa Borno ta yankin diffa zasu ɓulla Nigeria zuwa yanzu wataƙila sun kusan cimma sandamun Maraɗi , ai Ahmadou gayu zaƙaƙurin direba ne ,   " nufin ka dagga nan Fatima ta tai Borno ta yankin Diffa ? Yankin da yake cike da hatsarin ƴan tawayen Boko Haram suna kama mutane suna garkuwa da su bayan sun kashe wasu ? Bodar da take a rufe , sai ta ɓarauniyar hanya ake bi ? Shine kun ka turata baku hanata tafiya ba , ba kuyi yi la'akari da ƙarancin shekaru gami da rauninta na ɗiya macce ba ? Wani irin raruma ya kaiwa Dattijon kafin ya ankara ya ɗago shi , cewa yake ,   "ko waye direban kayi ƙiransa maza ya dawo da matata , kadda ya yarda ya jefa rayuwarta ga wannan mummunan hatsarin da kai da shi da zuri'ar ku baki ɗaya sai na ɗaure ku muddin wani mummunan abu ya afku ga matata , Da kyar mutane suka ɓanɓare hannuwan Youssouf daga wuyan dattijon nan da kawo lokacin numfashin sa ya fara ƙaƙarewa , Da ban baki gami da lallashi jama'a suka danni Youssouf ya nutsu aka nemo number Ahamdou gayu aka bashi ya shiga ƙira jikinsa sai tsuma yake , Da kyar ya samu wayar ta shiga , sai dai ko da aka ɗauka waƙar Barmani Mai-coge ce kawai take fitowa tarwai ta cikin wayar sai kuma iska irin na hanya ,   Ya dunga "Alo , Alo , Alo , Bai ji muryar kowa ba , ya kashe ya sake ƙira nan ma an ɗaga amma "Alo, Alo , kawai ake cewa daga ɗaya ɓangaren , duk maganar da yake yi ba'a jinsa , Haka ya dunga ƙira cikin gigita tsawon lokaci ba'a ɗagawa daga baya ma daina shiga wayar tayi , cikin tashin hankali ya ɗago kansa , sai dai duk mutanen da suke tare a wajen ya tarar babu ko guda sun watse, sai fa Yakaka da take durƙushe a ƙasa tana hawaye sai kuma Hajja da take tsaye ta rafka tagumi idanunta da guntayen ƙwalla , Rasa wanda zai sake tunkara yayi , dan haka suka jiyo gida idan banda kuka babu abunda Yakaka take yi , jin cewa Falmata ta hau hanya mai tattare da hatsarin ƴan Boko Haram , ya kaɗa ƴan hanjinta , Zuciyarta ta cika da tsoron sake rasa ƙanwarta , Youssouf ma tunda suka dawo gida kai tsaye sashinsa ya shiga yana sake gwada ƙiran layin Ahmadou gayu , sai dai har chajin wayarsa ta kai ga sauƙa bai samu nasarar sake samun layin ba , Ajiye wayar yayi lokacin da wasu hawaye masu zafin gaske suka sauƙo masa a karo na biyu cikin tarihin rayuwar girmansa , yayi kuka . *** Su Falmata sun kwana a wani ƙaramin gari dake yankin zinder kusa da garin Diffa , anan suka yada zango , cikin motar ita ta kwana yayin da sauran mazan suka fita ba tare da ta san ina suka yi ba . Asubar fari bayan tayi Sallah , suka sake damƙar hanya , tafiyar yini guda ta kai su ga kaiwa ƙarshen yankin diffa ta gabashi , inda suka sau hanya tare da nausawa cikin daji  , Gudun da motar take alhalin kan tuddai da kwari ne yasa motar take buga tsalle lokaci zuwa lokaci , da hakan yasa cikin falmata ya wani irin riƙewa tare da fara yin ciwo , ga buguwar da jikinta yake yi da motar , gami da warin sigari da bata san yaushe ya gauraye motar ba yana ƙoƙarin sanyata haraswa . Duk da bata gani sosai ta fahimci dare yayi saboda duhu da ya mamaye ɗan guntun hasken da idanun ta suke iya gani , ya zama dilum bata ganin kome . Sun kai kimanin awanni biyu a daji suna wannan gudun kafin ta ji motar ta tsagaita gudu , ta tsaya a hankali , Hasken da ya dallare mata idanu mai ƙarfi ne da yasa ba shiri ta jaa hijabin ta ya rufe mata idanu , gami da runtse idanun . Tana jin lokacin da duk na cikin motar suka fita harda shi direban , a hankali ta buɗe idanunta ta cikin motar tana iya ganin mutanen wajen dusu-dusu da taimakon hasken wasu manyan dogayen tociloli da suke hannuwan wasu gungun mutane , Abunda ya bata mamaki bai wuce ji da tayi sun juya harshe cikin yarenta ba na kanuri , tar-tar suke magana da Ahmadou gayu da sauran mutanen cikin motar da tunda tafiya ta haɗa su bata ji sun cika hira ba ko da kuwa a tsakaninsu ne , bare har ta fahimci yare su ɗaya .. Ba sosai ta kai ga Fahimtar maganganun su ba , har kawo lokacin da suka ƙaraso wajen motar , da hausa Ahmadou gayu yace ta fito za'a ɗau saƙo daga ƙarƙashin kujerar da take , Cikin sauri ta ziro ƙafar ta waje ta fito , cikin rashin sa'a ta gurɗe ta kusa faɗuwa , 'yarinya ki kula , Cewar Ahmadou , Muryarta na ƴar rawa tace "Baba inada matsalar ido bana gani idan dare yayi wajen babu ramuka ko ? " Au to to ashe ma musaƙa ce , to babu laifi , ai daman irin ki ake so marasa idon yarinya yau makantar ki ta miki rana , ko kuwa ? Ya juya ga mutanen da suke bayan sa yana tambayar su , amma babu wanda yace ƙala a cikin su , biyu daga ciki suka matsa jikin motar tare da fara ɗaga cikin ramukan kujerun motar suna fito da wasu ƴan madai-daitan kwalaye da basu cika girma ba , Falmata da ta durƙusa tana ɗan murƙususu saboda marar ta da take mata ciwo , ta cikin hijabinta tana iya hangen kwalayen da bata san da su ba a motar  kafin zuwa wani lokaci an tara su da ɗan yawa , Ɗaya daga cikin mutanen da fuskar sa ke naɗe da mayafi ya sunkuya tare da ɗaukar Ammo box ya buɗe ya zazzago wasu alburusai da suke ciki a jere , hannu ya miƙa na gefen sa ya miƙa masa tocilar hannunsa , ya haska harsashin sosai yana jujjuya shi a hannun sa , Cikin Falmata ya bada wani sautin ƙululu lokacin da ta ga an miƙo masa bindiga ya zura harsashin a ciki , wani irin tsoro mai girma ya ziyarceta , meye yaje shirin faruwa da ita ? aina ma wai take ? Magana suka fara yi bayan sun ɗan yi gaba kaɗan da inda take tsugunne ba tare da wani ya kulata ba daga cikin su , Tsantsar tsoro yasa ta daina fahimtar me suke cewa duk kuwa da cewa da yaren da tafi fahimtar sa bisa ga sauran yaruka suke magana  , idanunta sun fir-fito , bindigogin hannuwansu kawai take bi da kallo da zuwa lokacin ta lura fiye da rabinsu suna riƙe da bindiga . Da ɗaya-ɗaya suka jide kwalayen , tana ganin lokacin da suka ɗaga kujerar da take baya suka maida wata jakar bacco gurbin da suka cire kwalayen ,daga haka ta ga sunyi musabaha tsakanin Ahmadou Gayu da wasu daga cikin tawagar , Da gudu-gudu suka hau bayan motocin su ,suka tada tare da nausawa cikin daji . Amadou gayu ya ƙaraso kanta lokacin da yake cewa , " 'yar dindimi sai ki tasso mu tai na sauƙe ki daga bakin hanya inda zaki iya samun motar da zatta sada ki da cikin garin Maiduguri ni iyakatai bakin daji kome da kin ka ji motsi nai anan ki manta da sautin anan muddin kin biɗarwa kan ki lahia , kin ji kou ? Gyaɗa kai Tayi da sauri , ta shiga motar suka sake nitsawa cikin daji , sai lokacin ta lura babu kowa a motar sai su biyu , ko ina sauran mutane huɗu na bayan motar ? Ta tambayi kan ta . ** Ƙarfe sha ɗaya na safe yayi mata a cikin babbar tashar garin Maiduguri , bayan Ahmadou gayu ya sanya ta a mota daga ƙaramar hukumar Mobar da ta kawo ta cikin garin . Duk tayi busu-busu da ita ta fita hayyacinta , yunwa da firgici sun maida ita firka-firka , amma duk da haka . Hamdala ta dunga yi lokacin da ta samu tabbacin tana cikin garin Maiduguri ne ta samu ƙubuta daga hannun mutanen da tun-tuni ta fahimci ko su waye su . tunanin inda zata dosa kuma ya rufe ta , domin ita dai bata san takamai-mai sunan unguwar gidan Prof ba , duk rayuwar ta cikin garin ta yi ne a halin tana makauniya , Wata rumfa ta hango ana tuyar doya da ƙwai a bakinta,  ta ƙarasa ta zauna daga ƙasa tana kallom mutanen wajen da fiye da rabin su maza ne hatta mai tuyar da mai rabawar duk samari ne , Da zamanta a wajen , wani matashi da ya ciko ɗan farantin roban hannunsa da soyayyar doya mai kwai , ya mata duban ƙasƙanci , kafin ya ajiyewa wani mutum doyar a teburin gaban sa , ya ƙaraso inda take "Ke baiwar Allah ki tashi daga nan , idan bara za kiyi ki shiga cikin tasha ko kuwa ki nemi wani wajen amma ba nan ba wajen sana'ar mutane . 'kayi haƙuri dan Allah hutawa nake yi , ga kuɗina ka bani abunda kuke sayarwa na duka , Ta miƙa masa kuɗaɗen da bata san adadinsu ba da ta zaro daga cikin jakar hannunta , Kallon kuɗaɗen da bana Nigeria bane ya yi , kafin yace "waɗannan takaddun fa ? Kuɗin ina ne ? Kafin ya rufe baki ubangidansa ya ƙwalla masa ƙira    " Bashari wai kana ina ne ?wannan wanne irin tsagoron zunzurutun walaƙanci ne zaka tafi hirar banza ka barni da ayyuka , to wallahi idan har ƙazar nan ta ƙone a mai , na rantse sai ka biya ni dan ni da asara kullum saɓani muke . Da sauri Bashari ya bar kan Falmata ba tare da ya karɓi kuɗin da take miƙa masa ba , Ya ƙarasa da gudu wajen ogan sa , "kayi haƙuri oga wata mata ce kamar mahaukaciya dai haka ta zo da wasu kuɗaɗe kamar na landan a hannunta wallahi oga wai ta miƙa min su na bata doya , kuma kuɗin dayawa oga Da sauri Ɗanliti ya saki matsamin da yake hannunsa acikin mai ba tare da ya tsame doyar ba , "kai Bashari na fa sanka da sakin ƙwai , kuɗin landan fa kace ? Dala fa kenan ? Yau a masu sayen doyar tawa har da masu Dala ? Ina take ? Nuna min matar ? Nuno masa Falmata yayi da har lokacin take takure a zaune , Cikin ƴar marairaicewa Ɗanliti ya kwararo mata sallama , da sauri ta ɗago kanta jin muryar wanda ta taɓa sani a baya , Suka yi arba da fuskokin juna, shirun ƴan wasu daƙiƙoƙi suka gifta kafin Falmata ta miƙe tsaye da sauri tunowa da tayi da ko wanene Ɗanliti. ' wa nake gani haka kamar un-un Ɗankachallari ?  Wai kece ko kuwa kamanni ne ? Ah ai babu zancen kamanni ma ga ƙwala-ƙwalan idanun nan daga ina kike ƴarkachallari haka kamar 'yar bina ? Muryar ta na ɗan rawa , tace " Ba sunana ba kenan , sunana Falmata , ' haka fa ashe sunan ki kenan , to dawo daga nan a kawo miki doya ki ci ki sha ruwa ko kya samu nutsuwa , na ga yunwa na tanɗar bakin ƙirshirwa a fuskar ki . A ɗarare ta zauna a inda yake nuna mata kan wani benci , aka kawo mata zazzafar doya da ƙwai har da dafaffen ƙwai guda biyu da aka soya su da ƙwai , Tas ta cinye ta sha ruwan leda biyu , tayi hamdala Ɗanliti da yake gurin suyar sa ya bari tare da sake dawowa yana sake tambayar ta daga ina take ? A takaice ta faɗa masa daga inda take , daga haka tayi shiru Ɗan jimm yayi yana kallon ta , kafin yace " wai , tabɗi yanzu nan daga Niger kike ? shiyasa mana na ga kin koma busu-busu , ashe rairayin hamada ne ya turbuɗe ki , ai kin ma kaima barka da sahara bata haɗiye motar ta ku ba kamar yadda nake ji ana labari wai-wai , koda yake da kuma kun yi mutuwar shahadar nan da kowa ke nema , " nima kin ga ai yanzu duk na tuba na daina abunda yake jawo min tsinuwa , na kama ƴar sana'ata da nake rufawa kaina asiri da ita , aure ma nake shirin yi , O ni Ɗanliti mutuwar Saly Fara ta zamanto min alherin da na samu shiriya a domin ta ,   Ya ɗaga hannun biyu sama , yana ƙara cewa       "Allah na ƙara gode maka da ka kashe Saly Fara ni kuma ka shiryar da ni . Shiru Falmata tayi tana sauraren bayanin da bata nemi jinsa ba , ji tayi ya cigaba da cewa , " ai ƴar danginku ma zan aura wallahi kuwa , Ɗago kanta tayi ta dube shi , "ƴar dangin mu ? Tambaye shi da mamaki , " eh Ƴar uwarku Yagana ba , ni kuwa ina Yakaka wallahi habibiya tana nemanta ruwa a jallo tace tayi ta zuwa gidan da kuke bata samun ku , can gidan wani mutum mai kuɗi wai a Danboa road ko ina ? Da sauri Falmata tace ,   "Ina Yagana take ? ta san gidan Prof ? Ka kaini wajenta ta kaini gidan Prof , Kwantar da hankalin ki indai habibiya kike nema kin same ta tunda kika ganni , nan da mintoci talatin ma zaki ganta anan ta zo , ai tare muke sana'ar mu , ita take yi mana wanke-wanken farantan kayan sana'a , kinsa rayuwar nan cuɗanni na cuɗeka ne . **** Yagana ita ta sada Falmata da gidan Prof da misalin ƙarfe biyu na rana , har falon prof ta so shiga da ita sai dai aka hana su saboda yana tare da baƙi , amma an musu iznin shiga ciki sashin matar gidan domin su jira shi . "Falmata ai tunda na kawo ki ni zan iya tafiya ko ? Yagana take neman iznin Falmata bayan sun kawo ƙofar sashin su Rahima , "Yagana , Nagode , Nagode zaki iya tafiya , "Babu kome Falmata ai mun zama ƴan uwa banda sharrin shaiɗan da ya rinjayeni a baya na aikata kuskure , Dan Allah idan Yakaka ta dawo zan zo na nemu gafararta ta yafe min . Nan suka yi sallama ,ba tare da Falmata tasan wanne kuskure Yagana ta aikata ba da take neman yafiyar Yakaka , Jikinta babu ƙarfi ta nufi cikin gidan , a zuciyarta tana saƙa yadda zata yi ta tunkari Prof da zancen ya raba aurenta da Youssouf batare da ta bayyana mummunan laifin da suka aikata ba shi da Yakaka , Saboda bata so wasu su dubi Yakaka da wannan mummunan laifin , zata zama abun aibatawa a wajen Al'umma , A hankali ta tura ƙofar falon ta shiga sanyi da ƙamshi mai daɗi ya buso ta , daga ciki kaɗan ta tsaya tayi sallama da zazzaƙar muryarta , Cikin nutsuwa matar da take zaune a kan ɗaya daga cikin sabbin kujerun falon tana saƙa da zaren ul da kwarashi, ta ɗago kanta , idanun ta suka sauƙa akan Falmata da itama take iya hango alamun farar fatar ta daga inda take , Muryarta bata fita sosai ta amsa sallamar , Su dukkanin su shiru suka yi suna kallon juna , Cikin sanyin jiki falmata ta kalato murmushi ta ɗora bisa fuskar ta, zuciyar ta na bata cewa Rahima ce wannan take hangowa A hankali tace "Rahima ni ce fa, ni ce Falmata ƙanwar Yakaka baki gane ni bane ? Kwarashin hannun Khaalty Rahima ya faɗi ƙasa bata kula ba ta miƙe tsaye ta nufi inda Falmata take , zuciyarta na bata tabbacin cewa mafarki take , wataƙila kuma gizo take yi mata , Tana zuwa ta miƙa tafukanta biyu ta dafa kafaɗun Falmata idanunta suna jiran ɓacewar ta daga ganinsu , Ƴar dariya Falmata tayi , kafin tace , "Rahima kina mamakin gani na ko ? Yakaka ma ai tana zuwa wataƙila gobe zata iso ba tare muka zo ba Rahima.... Hannun Rahima da taji yana tattaɓa mata fuska , yasa ta haɗiye sauran kalmomin ta , ta riƙe hannuwan tana ƙoƙarin sauƙe su daga fuskarta , da wani irin sauti ƙasa-ƙasa , Khaalty Rahima tace "Falmatana ke ce ? Ke ce wannan Falmata ? Ke ce ? Ina Yakakana ? Rungumo ta tayi gaba ɗaya zuwa cikin jikinta tana fashewa da kuka mai sauti ... Assalamu Alaikum masu karatu . Da fatan duk kuna lafiya ?? Ina mai baku haƙurin ji na shiru da kuka yi wasu hidindumu ne suka sha kaina , da fatan kun min uzuri ? ❤ Nagode . [12/16/2019, 6:36 AM] +234 706 503 6187: MAFARI ( Hargitsin Rayuwa ) Umm'muaz 45 Da rashin yadda a fuskar Falmata , ta ɓanɓare jikinta daga na khaalty Rahima , Muryar ta na ɗan ƙyarma tace , "wacece  ? Rahima kece ? Zuwa lokacin Murmushi Khaalty Rahima take , murmushin da har ya bayyana haƙoranta , sake riƙe hannun Falmata tayi , da sautin muryar ta mai ɗan ƙarfi tace , "Falmatana ni ce Mamar ku , ni ce , ashe kuna raye Falmata , ina Yakaka ? Da wani irin yanayi Falmata take sake wara idanunta tana ganin dusu-dusun fuskar matar da take gabanta , tana jin wani irin bugu da zuciyarta ta sauya a take da ziyarta ruɗani a tare da ita tace, "Mama na ? Ke ce Maman mu ?    Sai tayi baya da sauri kamar zata gudu , ta waiga dama da hagunta , da wani sauti tace , "Yakaka ina kike ? Kina ina ? Ki zo ki ganta wai wannan Maman mu ce ? Wai da gaske ita ce ? Murmushin fuskar Khaalty Rahima bai ɗauke ba lokacin da hawayen fuskarta suke cigaba da sauƙa ta matsa tana sake kusantar ta , sai ta miƙa hannu ta jaa hancin Falmata da bai wani ciƙa tsayi ba , ta zarce da riƙe kumatunta duk biyu da hannuwanta , sannan ta haɗa goshin su guri guda , tana sake cewa ,"Ni ce Mamanku Faɗimah-Zahra ni ce Ina Amina ? Wani irin yanayi ne na zallar Farin-ciki mai tafe da sanyi mai samar da nutsuwa ,  taji yana bin duk wata jijiyar jikinta , a sanyaye ta karkata kanta , muryarta da rangwamen sauti tace ," Maman mu ke ce ? Ke ce Mama da gaske ba mafarki ko gizo ba ? Mama daman kina Raye ? Mamana .    Bata jira ta amsa mata ba ta zarce da rungumeta ,tana sakin kuka da ƙaramin sauti , irin kukan da Ɗa yake irin sa a lokacin da ya tsinci kansa a gaban Mahaifiyar sa bayan tsawon lokacin da ya ɗauka yana haɗiyar baƙin-ciki cikin kewar ta .   Khaalty Rahima ta sa hannu biyu ta rumgumeta , tana jin wani irin tarin farin-ciki marar misaltuwa , ashe daman rayuwa zata sake iya yi mata sauyi mai tattare da farin-ciki irin wanda ta fidda rai da samun sa , ashe watarana zata zo da zata sake ganin ƴa'ƴan ta ? Allah abin godiya .    Sauƙowar Amnee daga Sama ita ta jaa hankalinta, da mamaki ta ƙaraso tana kallon su , da har zuwa lokaci , Falmata take kwakume da Mamanta bata bar kuka ba , da alamar tambaya a muryarta tace    "Ukhtee Rahima me ya faru ? wacece wannan ? , jin sautin muryarta yasa Falmata ɗago kanta , kafin ta bi bayan Khaalty Rahima da take riƙe da hannunta , suka ƙarasa gaban Amnee , da murmushi Khaalty Rahima ta haɗa hannun Falmata da na Amnee , tana cewa    " wannan ita ce 'Ya ta Falmata da na baku labarin su ina zaton sun mutu ita da yayar ta mai sunanki Amina da ake mata laƙabi da Yakaka , ikon Allah da girma sai ga shi ya kawo min ita har gabana .      Sai ta waiga ga Falmata , tare da cigaba da cewa , "Fatima ya akayi kika san ina nan ?   Da bayyanuwar murna Amnee ta zarce da rungume Falmata , kafin ta ɗora da cewa , Alhamdulillah , Alhamdulillah , ashe ba haka nan ba na so yaran nan tun a rana ta farko da na fara ganin su , ace 'ya'ya nane , jini na , 'ya'yan 'yar'uwa ta , Ukhtee Rahima ai nasan Fatima da Yakaka tun shekarun baya suke rayuwa tare da 'yan uwansu a gidan nan ba tare da sun san dangantakar su da juna ba , kai Alhamdulillah . Saman kujerun wajen suka zauna ,suna sanya Falmata a tsakiyar su , khaalty Rahima ta ce ,      "Ikon Allah Ukhtee ashe ma kun san su ? Ashe suna hannun ku ?     " ƙwarai na san su , ai yayan Zainab ( Doctor Hamza )  shine ya kawo su gidan nan a matsayin ƴan gudun Hijira , a gidan nan suke tsawon shekaru kusan biyar zuwa shidda  ,  ikon Allah kenan ai kuwa  ko zuwan Yakaka na kwanan nan taje har wajena ta gaishe ni ,  ai itace wacce kika ji na tambayi Rahima shekaranjiya kan ina take ta shaida min ta tafi Niger wajen Ƙanwar ta da 'yar ta , Allah ya saɓa haɗuwar ku ai da gidan nan zaki tarar da ita .    "Ikon Allah ,  to Alhamdulillah , Alhamdulillah , sune kalmomin da Khaalty Rahima take faɗi farin-ciki na sake gauraya ta , ji da tayi ashe ma 'ya'yan ta gida suka dawo , ashe ma tare suke da yayun su , ƙarƙashin kulawar mutumin da yake mazaunin Uba a wajenta , Babu shakka tare da dukkanin tsanani akwai sauƙi , kuma ba'a fidda rai daga Rahamar Ubangiji .   A kusan tare suka jefawa Falmata tambaya ,     "Fatima ina Amina da 'yar ta ? Shiru Falmata tayi da famin raunin cikin ranta , a hankali ta ce da su ,     "Allah ya yiwa Mama rasuwa kwanaki huɗu da suka wuce ,    "Innalillahi wa inna ilaihi raji'oon,  Innalillahi wa inna ilaihi raji'oon,"  suka haɗa baki wajen cewa , shiru kuma ya gifta tsakanin su cike da jimamin rashin jikar su da basu kai ga samun damar ko da ganin fuskarta ba a zahiri , babu shakka Allah baya barin wani domin wani ya ji daɗi .    " Ina Maisunan Ukhtee ita kuma ? Ba wajen ki ta tafi ba ?       Ƙhaalty Rahima ta sake tambayar Falmata ,    Shiru Falmata tayi tana sunkuyar da kanta ,   Wani busasshen yawu Khaalty Rahima ta haɗiye tana jin tashin hankalin da yake farmata , kada dai ace wani mummunan lamari ne ya afku ga ɗiyar ta mafi soyuwa gareta ?     Matsa hannun Falmata dake cikin nata tayi da ɗan ƙarfi , ta ɗan ɗaga sauti tana sake maimaita tambayar " Falmata ina kika baro Yakaka ?? *** A Niamey tunda Yakaka ta dawo daga tasha , bayan samun tabbacin Falmata ta riga ta tafi Nigeria ta wannan mummunar hanyar mai cike da hatsarin ƴan kungiyar Boko Haram , bayan kuka babu abunda take yi , gabadaya ta ɗora laifin gudun Falmata akanta , tayi danasanin zuwanta ƙasar baki ɗaya yafi a ƙirga , ganinta da ace bata zo ba da Falmata bata gudu ba , sai ta ji inama da ta zauna akan batun Youssouf da yace su rufa asirin tsakanin su kada Falmata ta sani a tun farko , ƙila da suna da damar da zasu haɗu ita da Youssouf su wanke kansu a wajen Falmata bayan sun ƙaryata ƴan uwansa a gabanta ,  da kuma lamarin bai kwaɓe ya haka ba , Ganin kuka ba zai mata magani ba yasa ta miƙe tsaye ɗauke da jakar kayanta , Hajja wacce take zaune zugum ta dube ta tare da cewa ,      "Babba uwar Mama ke kuma ina za ki ? Kadda kice min kema gudun fanfalaƙin za kiyi ? Kiyi wa Allah ƴar nan ki tsaya mu ji da damuwa ɗaya kadda ki ɓaro mana wata sabuwa , guje-gujen nan ba kana bane , 'ya'yan nan ai ƙwarya ta gari tana ragaya , kamar yadda darajar ɗiya mace ɗakin Mijinta kar ki tafi ko'ina Dan Allah , Ba tare da Yakaka ta dubi Hajja ba tana share hawayenta da gefen hijabinta tace , "Hajja gara na tafi saboda Falmata fa ko da taje Maiduguri lafiya , bata fa san hanyar gidan Baa prof ba, kuma bata san kowa ba a garin bayan shi , dole zanyi hanzarin tafiya nima ko Allah zai sa na haɗu da ita a tasha , na tarye ta Hajja ina ƙaunar Falmata ita ce kaɗai jinina a duniya ina tsoron rasa ta Hajja , zan tafi bazan iya zama ba nima . Guntuwar ƙwallar da ta tarawa Hajja a ido ta sa hannu biyu ta shafe fuskarta ta muttsuƙe , " To Shikenan Yakaka tunda kin ce haka bari nima na haɗa ƴan kananun kayan buƙatu na mu tafi tare , ai nima zama bai ganni ba , to na zauna nayi me ƴar nan ? Ai tunda ganga ta fashe sai ƴan rawa su watse , Da hanzari Hajja ta shiga harhaɗa kayanta, tana cewa ,        "bari na tafi da waɗanda dole zan iya buƙatar su , sauran kuma idan Allah ya min dawowa na cigaba da Amfani da abuna idan kuwa ma tafiyar kenan , to a biyo ni da tsunmokara na , wannan lamari dai da ɗaure kai yake babu shakka da walakin wai goro a miya . Yakaka da har lokacin a tsaye take akan ƙafafunta bata ce da ita ƙala ba , Cikin ƴan mintoci kaɗan ta haɗe kayanta a cikin wata babbar jakar matafiya da Youssouf ya taɓa saya mata , tana shirin yafa mayafinta suka tsinkayo sallamar Youssouf daga ƙofar falon , Hajja ta amsa tana nufar falon A tsaye ta tarar da shi shirye tsaf cikin riga da wondo na kaftani da ya sha aiki irin na saraki , ba tare da ya yadda Hajja ta ga ƙwarar idanunsa ba fuskarsa babu walwala ko kaɗan sai tarin damuwa da tashin hankali da suka bayyana kansu ɓaro-ɓaro , cikin Amonsa da a yau ya sake kaurara da buɗuwa yace     "Hajja ni zan tai Maraɗi yanzou Hajiya Umma tai ƙirana , don Allah ku zauna a gida har na kai ga dawowa nan da kwanaki biyu , lamarin Fatima kouwa zan yi dukkanin ƙoƙarina da Yardar Allah babu abunda zai samu Matata da abinda ke cikin ta . Ɗan karkata kai Hajja tayi da sigar tausayawa tace , " Babban soja Allah ya tsare hanya , sai dai kuma yanzu na gama fama da ita yayar Falmata kan cewa da tayi a yanzu itama za ɗau hanyar Nigeria saboda ko Allah zai sa su gamu da ƴar uwarta a tasha idan sun isa Maidugurin dan ita Maiɗakin naka ai kasan bata san ko'ina ba a can ko gidan shi mariƙin nasu bata sani ba , ana gudun kar ta ɓata ko ta shiga wani mawuyacin hali kuma a can , da naji haka sai nace to fa nima zama bai kamani ba tare zamu tafi , to kaga shirin nan da nayi ma na tafiyar ne ga kayana ma can na haɗa su gu ɗaya . Bayan ya gama sauraron Hajja da tayi shiru tana tsumayen iznin sa , sai yace ,     " hakka ma shawarace mai kyaou Hajja , to idan hakka ne ku taho na sauƙe ku ga tasha na sanya kou a mota , nima sai na tai gida ,    "Amma Hajja doumin Allah dagga kun cimma gida kun tadda Fatima ki sanar min ta téléphone , sabadda na san halin da kuke ciki a can , duk da nima ba da jimmawa ba zan tai can Nigeria ɗin , kuma a nan sojin mu zasu yi bakin ƙoƙari wajen duba hanyar da ita Fatima zasu bi , sai dai kouma idan har ta ɓarauniyar hanya ta daban zasu ɓulla yanzou fatan mu dai yana ga Fatima ta cimma gida lahia . " to babu laifi Babban soja ai sai mu tafi ɗin , Allah dai ya sassauta wannan lamari , bari na ƙira ita Yakaka , Mota ɗaya suka tarar wacce zata tafi Kano kai tsaye daga Niamey dan haka Youssouf ya biya musu gidan baya na motar su biyu rak da daman mutum ɗaya suka tarar a gaban motar dan haka nan take aka shiga neman direba ya zo kuɗin kujerun mota sun kammala , Laluba aljihunsa yayi ya fiddo kuɗaɗen ciki da baki ɗaya CFA ne , mayar da su aljihunsa yayi saboda sanin da yayi daga sun bar shiyar ƙasar su ba zasu musu wani amfani na sosai ba , ya zaro wallet ɗin sa da dalolin Amurka ke ciki a miƙe , ya matsa kusa da gilashin motar da yake sauƙe ta sashin da Yakaka take , Ba tare da ya dubi fuskar ta ba yake miƙa mata kuɗin da bai riga ya ƙirga ya san adadinsu ba , Yakaka wacce tunda ta shiga motar ta ɗauke kai daga barin kallon sashin da yake tsaye , amma tana ankare da shi ta kuma ga tsayuwar sa akanta yana miƙa mata ƙudi , bata son sake kallon fuskarsa ne dan haka taƙi ɗago kanta , Hajja wacce take raba ganinta a tsakanin su biyun , ta ɗan zunguri Yakaka ,   "Babba uwar Mama , Babban soja yana baki saƙo ,   Da wani irin yanayi na gargaɗi a fuskarta ta kafe Hajja da idanunta da suke da kaifin kallo masu kamar gilashi ,   Galala Hajja tayi tana mayar mata da martanin kallonta , sai kuma ta muskuɗa ,tana cewa "Ajabba inji kanurai, o ni hauwa'u ,    sai kawai ta maida ganinta can gefe tana kyeɓe baki . A hankali Youssouf ya zura hannunsa kaɗan ta cikin motar ya sauƙe mata kuɗaɗen akan cinyarta yana cewa "Hajja Allah shi kiyaye muku hanya don Allah Hajja duk yadda lamari ya kassance muku ki jisheni , " Amin Amin Babban soja , da yardar Allah zan sanar da kai duk yadda ake ciki , kaima kuma Allah ya tsare maka hanya , mungode , mungode sosai Allah shi yiwa rayuwa Albarka . "Amin Hajja nima nagoude , yace yana kama hanyar barin wajen , Yakaka wacce tunda ya ajiye mata ƙuɗin ta runtse idanunta tana tuno da lokaci na farko a haɗuwarsu , yadda ya ajiye mata kuɗin da ya sayi martabarta da su akan cinyarta ya haka ,     Hannunta ta kai tana ture kuɗin da ya ajiye mata a yau zuciyarta cike take da rauni mai tarin yawa , sanin da tayi a yanzu Youssouf ya haramta a gareta , ta kuma Haramtawa kanta shi koda kuwa babu ran Falmata .       Tashin ƙugin motar su yazo dai-dai da sauƙar hawaye a idanunta , haƙiƙa so gaskiya ne , so halitta ce da Allah yake sarƙawa a tsakanin zuciyoyin bayin sa domin ya samar da Salama a tsakanin ƴan Adam , yafiya , haƙuri tare da tsusayawa tafe suke a cikin so na domin Allah , Babu shakka Youssouf shine mutum ɗaya da Allah ya ɗarsa mata son shi tun bata san menene so da kansa ba , ta kuma so shi ba domin kome da ya mallaka ko ya taɓa mallaka mata ba , cikin rashin sanin ta jarrabawa ce Allah yayi mata kan soyayyar sa ,    Tun ranar da ta san laifin da Youssouf yayi mata kan Yaudarar ta da yayi ya ɓata mata rayuwa bata taɓa jin tsanar sa tsana irin ta ƙiyayayya ba , sai dai ta ji tsanar shi bisa ga laifin da tasan ya aikata mata, take kuma neman yadda zata yi ta hukunta shi domin ta goge wannan tsanar da tayi masa a dalilin laifin sa , Dawowa da tayi ta tarar ya auri Falmata , ya rugurguza mata zuciya , lamarin ya girgiza ta fiye da duk wani abu da ta taɓa cin karo da shi cikin rayuwarta , Tashin hankalin da ta hango tare da Youssouf lokacin da tayi tattaki ta same shi take masa togaciyar ya saki Falmata , tare da tirjiyar da yayi mata sun shaida tare da bata tabbacin cewa Youssouf yana son Falmata , so kuma mai  tarin yawa , abunda ya kassara mata duk wani karsashin ta ,  ya kuma ƙara mata hau-hawar ɓacin rai ,zuciyar ta ta shiga tuhumar ta kan yaya zai yi mata haka ? Rana ta farko da ta san da tabbatuwar cikin jikin Falmata sai ta ji ta tsani kanta tana kuma tir da zuciyarta da ta gagara yakice shi baki ɗaya daga cikinta , alhalin tuntuni ya zama mallakin ƙanwar ta , A yau saƙo-da-lungu take bi tana zaƙulo duk wani ɓurɓushi na son sa tana zarewa daga cikin ranta  , duk wani gurgun tunani ko hasashen da ta dunga yi a baya na zasu dawo suyi rayuwa tare da ita da shi da ɗiyar su har ma su haifi wasu ƴa'ƴan ,  yana zagwanyewa tare da gogewa daga cikin ƙwaƙwalwarta , ta rabu da Youssouf da sunan so kamar yadda Allah ya rabata da Mama , Youssouf ba nata bane ,  ya taɓa zama nata ne kaɗai akan shimfiɗar da shaitan ya shimfiɗa musu . Youssouf na Falmata ne tare da ƴa'ƴan da zasu haifa nan gaba da kuma sauran matansa , Takurewa tayi a jikin ƙofar motar tamkar zata tsaga ta koma ciki saboda wani irin zogi da zuciyarta ke yi , babu shakka cikin sadauƙarwar soyayya ta gaskiya akwai ciwo mai tsanani . *** Ya juya tare da tarin tausayinta cikin ransa , yaso ko da sau ɗaya ta bashi dama ya nemi yafiyar ta bisa ga laifin da shi yasan ya aikata mata , har abada ita ai uwa ce ga ɗiyar sa mafi soyuwa a gare shi , bai so ba suka sake yin rabuwa makamanciyar ta farko , A shekaru da girma gami da hankali nashi irin na cikakken Namiji , ba sai ita ko wani ya taɓa faɗa masa cewa tana son shi ba so kuwa mai tarin yawa da shi yake iya hango shi a kwance cikin idanunta ɓaro-ɓaro koyaushe ta dube shi ,  Sai dai shi da ita dukkanin su sun faɗa ne ga jarabawar rayuwa , kuma shi bai mata so irin na auratayya ko kaɗan , sai dai yana tausayawa mata sanin yadda ciwon so yake ,ga wanda duk Allah ya jarabta . gefe guda kuma yana jinjina Yakanah irin tata da bata taɓa furta masa kalmar so a gaban sa ba ko sau ɗaya , ta kuma yi ƙoƙarin dannewa ta ɓoye hatta ga shi kansa bata yadda cikin saninta ta nuna abunda ke binne cikin ranta ba , bare kuma ga ƙaunarta da yasan abadan baza ta taɓa bari ta fahimata  , daga ƙasan ransa ya furta "Madallah da ƙarƙƙarfar kyakkyawar zuciyar da take iya danne tasirin So , ƙwarai ita ɗin ai jaruma ce . " Ƙarfe uku na ranar ta yi masa a cikin Masarautar su inda ya tafi kai tsaye ga fada ya kai gaisuwa gurin Maimartaba wanda ya amsa masa fuskarsa ba yabo babu fallasa , sai dai saɓanin baya da idan har ya shigo fada ƙirarin da manyan fadawa da kansu ke yi masa har ya tashi , yau dai shiru babu wanda ya kambama shi da ƙirarin sai fa dogarai da suke tsaye daga bakin-fada . Shiru yayi kansa a sunkui yana jiran Maimartaba yayi masa umarnin dawowa daga gefensa kusa kamar yadda ya saba a koyaushe , sai dai har ya kusan mintoci ishirin a zaune maimartaba bai sake duban sa ba , dan haka ya miƙe yana mai sallama da Maimartaba da sauran jama'a da suka amsa a sama-sama , Idanunsa suka kai inda yake mazauninsa ada kusa da ƙafafun Maimartaba , karaf suka haɗa ido da Mammadou da yake zaune a gurbin sa , wanda yake jifan sa da wani ɗan guntun murmushin ƙeta , ɗauke kansa yana ƙarasa barin Fadar . A sanyaye ya taka yana yana nufar ciki sashin Hajiya Umma , a hanya babu abunda ya sauya na yadda bayu ke zubewa gaishe sa , sai dai yana lure da wani irin kallo da wasun su ke binsa da shi wasu kuma yana iya jiyo ƙus-ƙus ɗin su daga ya gota . Ita ɗaya ya tarar da ita a falonta na ƙurya da yawanci sai zata yi ganawa ta sirri take shigarsa , Zama yayi a gabanta yana mai sunkui da kai cike da ladabin da yake halayyar sa ya gaishe ta , muryarta babu amo sosai ta amsa gaisuwar sa , Shiru ya ɗan gitta kafin da murya mai kaushi tace da shi ,     " Ina kouma itta ɗiyar da kake amren ? Shiru yayi kaɗan kafin ya ce      " sun tai ga ƙasar su baki ɗaya , Sake tsare shi da ido tayi , duk kuwa da ta ɗan yi farin-ciki da cewa da yayi "sun koma ƙasar su , sai ta ɗora da cewa  " ka sau amren ta ko kuwa ?    Shiru yayi cikin fargaba , yana tsoron kadda ta tilasta shi ya saki Fatima , wani sashi na zuciyar sa ya ji yana gargaɗin sa daga sake yin ƙarya , wani busasshen yawu ya haɗiye , ya ɗago da kansa ya dube ta , a hankali ya mayar da kansa ƙasa kafin yace ,     "Ban sau amrenta ba sun tai gida ne kafin al'amura su dai-daita anan , "Youssouf ,    Hajiya Umma ta ƙira sunan sa , a tsorace ya amsa "Na'am Umma , zuciyarsa tana mai tsananta bugu yauce rana ta farko a iyakacin sanin sa da ta taɓa ƙiran sunan sa kai tsaye .   " na maka oumarni ka sau amren ɗiyar nan ka aika mata da shikan ta can zouwa ga ƙasar su , muddin kana ƙamnar da na yafe ma kouma Mahaifinka shi maka afouwa , idan kouwa ka ƙi bin umarni na Youssoufa , shiru tayi bata ƙarasa ba ,    sai dai ya fahimcin munin abunda ka iya biyo baya ganin yadda ɓacin rai ya ƙara hauhawa a kan fuskar ta bayan ta kawar da kai daga barin duban sa ,    Gumi ne ya shiga keto masa kota'ina cikin jikin sa , ya sanya hannun sa yana share zufar goshinsa ,    Muryarsa can ciki yace , " Na amshi oumarnin ki Umma, ki yafe min bissa ga kuskuren da na aikata . Muryar ta da ɗan sassauci tace , " Laifin ka ga Allah kayi ka nemi Yafiyar sa , doumin shi mai yawan afouwa ne ga bayinsa ,  sannan ka kyautata tuban ka , ni kam abou ɗai nake so kayi shine sakin auren ɗiyar nan idan kayi hakka shikenan .   Shiru yayi baice kome ba , saboda zallar tashin hankalin da yake ciki , duk wata ƙafa ta isar da saƙo a jikinsa jinya take da amsar umarnin Hajiya Umma .   Ganin yadda ya zamto tamkar wanda aka zarewa lakka a gabanta yasa tayi gyaran murya tana mai ƙarfafa zuciyarta daga tausayi irin na tsakanin ɗa da mahaifiya daya soma mamayarta , musamman kasancewarsa mafi soyuwa a gareta cikin 'ya'ya ,     " ka tashi ka tai ga matanka bayan ka tanadi kyawawan kalmomin da za ka yi amfani da su wajen tausasa zuciyar su doumin laifin ka mai nawi ne a wajen su . Kamar jira yake tace ya tafi , sai ya miƙe a hankali bayan ya mata bankwana ya fito daga falon , baya sanin takamaimai ina yake jefa ƙafarsa ya nufi shiyar gidan sa , Sashin Siyama ya tasarwa ba tare da ya haƙiƙance meye zai je ya sanar da ita ba , Da shigar sa Yumna ta taso da gudunta daga inda take wasa a tsakiyar falon da tarin kayan wasanta ,   Da sauri ya sunkuya ya ɗauke ta yana matse ta a cikin jikin sa kewar Mama marar adadi na taso masa ,    "Papa ,    ta ƙira shi da ƴar muryar ta , "Yumna , ya amsa yana ɗora idanunsa akan Siyama da ta miƙe tsaye daga kan kujerar da take kishingiɗe Rakiya na mata tausar ƙafafunta , Da sauri Rakiya ta miƙa gaisuwar ta kafin ta bar falon zuwa can waje sashin su na ma'aikata , A hankali Siyama ta tako gaban sa bayan ta ƙirkiro wani guntun murmushi akan furskar ta , "Sannu da zouwa Biyamuradi,  da fatan ka iske mou lafiya ?   Tana ƙarasowa ta kama hannun sa guda , kafin ta cigaba da cewa ,     " Mu tai kayi wanka Baban Yumna kafin a samar da abinda zaka taɓa , Yanayin rashin kuzari bai bar shi ba ya bi bayanta zuwa sama ɗakinsa , Bayan ya yi wanka ya shirya , cigaba yayi da zama akan kujerar ɗakin ya zurfafa cikin tunanin umarnin Hajiya umma , da kowacce daƙiƙa guda tashin hankalinsa daɗuwa yake , gefe guda ga rashin sanin takamaimai halin da ita kanta Fatima ke ciki tare da ɗiyansa dake maƙale a marar ta ,    Ƙarar wayar sa ya sanya shi janye tagumin da yayi ya ɗau wayar ganin mai ƙiran nasa daya daga cikin manyan kwamandojin sojin su ne na yankin Diffa , Magana suka sake yi kan tsaron da zasu daɗa a tsakanin boda saboda motar da take ɗauke da matarsa da zasu bi ta Boda zuwa Nigeria , bayan ya gama wayar da bai ɗau lokaci yana yi ba ya ajiye wayar a gefe yana baya da kan shi ya ɗora kan bisa  allon kujerar ya ɗora dogayen ƙafafunsa akan ɗan teburin gilashi da yake gaban sa , Idanun sa ya runtse yana jin yadda kansa  ya ke sara masa musamman ta goshin sa ,    Siyama wacce ta ji shirun sa yayi yawa bayan ga abinci ta haɗa masa a shiyar cin abincin su , sai ta miƙe ta hau saman , cikin ranta kuwa ƙoƙari take tayi aiki da shawarwarin da Rakiya ta bata na danne kishinta daga barin bayyana shi a sarari , Tana murɗa ƙofar ɗakin ta hango shi a kujerar ya dafe kan sa da hannunsa guda , wani irin yanayi na zallar tausayi da ake samu ga abunda ake ƙauna ta gaskiya , shine ya tsigar mata , babu shakka a tun shigowarsa ta fahimci tsananin tashin hankalin da yake ciki . Bai ji shigowarta ba har zuwa zaman ta a gefen sa , sai da ya ji hannunta mai tsananin taushi ta ɗora akan nashi hannun da ya dafe goshinsa da shi ta janye shi ,   "Baban Mama , ta ƙira sa , ɗas ! Zuciyarsa ta buga da jin sunan Mama da ta masa inkiya da shi da Falmata kaɗai ke ƙiransa da sunan ,  sai ya dawo da ganin sa kanta ,bayan ya gyara zamansa yana jin wani irin yanayi mai tasari matuƙa ,    "Baban Mama ina miƙa ta'aziyyata kan rashin da muka yi na ɗiyar mou , Allah shi jikan Mama shi sa ta ceto mou . Sai tayi shiru tana neman dai-daita nutsuwar zuciyar ta daga tarin baƙin-cikin da yake bijiro mata na zallar kishin Falmata , ta ɗora da cewa ,    " Ina ƙamnata Fatima ? Da fatan ka baro ta lahia ? Da wani irin yanayi ya matse hannunta dake cikin nasa , cikin muryar dake cike da rauni yace     " nagoude sai dai a halin yanzou Fatima ta gudou ta barni zuwa kan hanya mai matuƙar haɗari , Hajiya Umma kuma ta min oumarni na sau amren Fatima , ki min addu'a Siyama lamura agareni sun tsaurara , kowa ba shi fahimta ta bisa jarabawa ta rayuwa . Ƙwalla ta ji sun tara mata a ido , tunda take bata taɓa ganin Biyamuradi cikin halin ɗimuwa tare da rauni makamancin haka ba , sai fa yau ta dalilin ɗiya Mace , babu shakka wagga ɗiya Fatima ta kai ayi gangamin tafiya kallon ta . Gagara cewa kome tayi illa kanta da ta kwantar bisa ɓarin jikinsa , cikin tausayin kai tace , " kayi haƙouri da ikon Allah lamura zasu dai-daita maka a tsakanin hakka nayi Alƙawarin taya ka da addu'a , Allah shi dawo maka da Fatima-zahra . Hannunsa duk biyu ya sa yana rungumeta tsam a jikin sa , ransa cike taf da ƙauna ta musamman gami da ƙarin ganin ƙimar ta a idanunsa , babu shakka shi masoyi na gaskiya abun riƙo da hannu biyu ne . " Nagoude ƙamnata kouma Matata , ya furta hakan yana sumbatar kan ta ,     Idanunta ta runtse da hakan ya bawa ƙwallar dake cike a gurbin idanunta damar zubowa , tana sauƙa akan kirjin sa . Kanta take tausayawa yadda zuciyarta ta afu ga son maso wani irin haka , ta san zafi da raɗaɗin rashin abun so dan haka take tausaya masa babu shakka ita bata da makaman yaƙin tunkarar ko wacece wannan Fatima da ake ta ƙiƙi-ƙaƙa akan ta da ta sanya Mijinta ya ɗimauce tare da jan ɗamarar yaƙi da duk wasu masu son shiga tsakanin sa da Abar son sa , labarin kome da ya faru tuni ya iske ta ta bakin Ubbo , Da tundaga lokacin tayi kuka tare da jimaminta ta har ta kusa faɗuwa jinya da taimakon Mai aikinta Rakiya da ta riƙa tamkar ƙawar shawarwarin ta , ta samu dawowar nutsuwar ta da Rakiya tayi ta bata shawarwari masu inganci tare da kwantar mata da hankali . " Baban Yumna mu tai ka ci abincin ,   " Bani jin Yunwa yanzou sai ko anjima kaɗan ,   Bata ƙara cewa da shi kome ba ta miƙe , tana barin ɗakin , zuciyarta baza ta juri ganin sa haka cikin ciwon son wata daban ba . Haka Youssouf ya ɗebe awanni cikin yanayi na bacci-bacci ido biyu , ( yayi likimo😂 ) Zuwa gefen la'asar ya sake yin wanka tare da shiri ya tafi Masallaci. *** Nan ya cigaba da zama yana addu'o'i tare da karatun Alkur'ani har zuwa shigowar lokacin Sallar magariba , da idarwar sa ɗan sako ya zo masa cewa Maimartaba yana son ganinsa a can turakar sa ta ganawa da baƙi . Da azama ya miƙe ƙarƙashin jagorar ɗan aiken suka cimma turakar Maimartaba , inda ya tarar da shi , shi kaɗai . Bayan sun sake gaisawa yayi shiru a zaune , daga ƙasa gaban kujerar da Maimartaba yake zaune , An ɗauki lokaci Maimartaba yana kallon shi baice da shi ƙala ba , yana nazarin tashin hankalin da ya bayyana a suffar sa , sai bayan wasu ƴan mintoci yayi gyaran murya   "Youssoufa , ya ƙira sunan sa ,    "Na'am ranka shi daɗe , yace yana sake ƙan-ƙan da kai ,    "Matso kussa Youssouf ka samrari abounda zan ce da kai , Da sauri ya muskuɗa ya dawo kusa sosai da ƙafafun Maimartaba, Cikin muryar da take cike da ilhama tare da tarin ilmi maimartaba yace ,"Youssoufa  sa'ad da Ubangiji ya tsawatar maka ka mai da hankali sosai, ka kuma yarda da gargaɗinsa, Ubangiji yana tsawatar wa waɗanda yake ƙauna. Kamar yadda mahaifi yakan tsawatar wa ɗan da yake fa'ariya da shi, "Kada ka zurfafa wajen biyewa tunani tunane-tunanenka mafarin rai ne kansa, ka kiyaye su abin mallakarka ne mafi daraja, "Kada ka faɗi kowane abu da yake ba na gaskiya ba, kada wani abu ya haɗa ka da ƙarya, ko maganganun ruɗarwa, ka duba gaba sosai gabanka gaɗi, ba tsoro ka tabbata ka san abin da kake yi, duk abin da kake yi kuma zai zama daidai , Idan har kayi haka ? ba za ka ji tsoro, sa'ad da kake kwance a gadonka ba, za ka yi ta sharar barci a dukan dare, ba za ka damu da masifar da za ta auko farat ɗaya ba, irin wadda takan auka wa mugaye kamar hadiri , Ubangiji zai kiyaye ka. Ba zai bari ka faɗa cikin tarko ba jinkirtawa yayi ya nisa tare da gyara zama , ya kai dubansa ga Youssouf wanda  fuskarsa tayi jaa idanun sa suka ciki-ciki . Ya cigaba da cewa , " Kada ka yadda Mazinaciya ta sake ruɗar ka , kada kayi duba ga ƙilbasar ta ko kuwa daɗi na daga kalmomin hilatar da suke kan harshenta.    "Leɓunan matar wani, mai yiwuwa ne, su yi zaƙi kamar zuma, sumbace-sumbacenta kuma su fi man zaitun taushi , amma ka sani bayan an gama , duka ba abin da za ta bar maka sai baƙin ciki, da azaba , za ta gangara da kai zuwa lahira, hanyar da take bi hanyar mutuwa ce ba a kan hanyar rai take ba, tana ragaita nesa da hanyar, amma kai ba ka ankara ba , " kayi nesa da zina Youssoufa kada ka yarda ka sake kusanta kan ka da zina Idan kuwa ka ƙi girmamawar da ake yi maka za ta zama ta waɗansu , mazinata ba kome bane su face walaƙantattu ababen walaƙantarwa ,            "Ka iya rungumar wuta a ƙirjinka sa'an nan ka ce ba za ta ƙone tufafinka ba? Ka iya tafiya a kan garwashi sa'an nan ka ce ƙafafunka ba za su ƙone ba? Haka yake da mutumin da ya kwana da matar wani , duk wanda ya aikata wannan, zai sha wahala . "kuma ai a yanzu ka gani , ka ga bala'in dake cikin zina , kome na tsanani da ya sabko maka ka sani cewa kankarane na daga zunuban ka ,zunuban mutum tarko ne, komar zunubinsa ce take kama shi , kayi gaugawar tuba ga Allah kafin lokaci shi ƙure maka .    Zuwa lokacin hawayene ke sauƙa a idanun Youssouf , nadama marar iyaka ta sabko masa , daga can ya tsinkayi muryar Maimataba yana sake cewa ,    " ina ka baro ɗiyar mutane da kake amre ?     Muryarsa na rawa yace    "ta tafi ƙasar su , kouma a yau Umma tai oumarni da na sau amren ta , zan sake ta Ranka shi daɗe , Ɗan murmushi Maimartaba yayi kafin yace ,     "mata sai abar su da lamarin su na ƙarancin hikima da tunani , anya ana gyaran ɓarna da ɓarna ?  Tafeeda ya gwada muna duk wasu shaidu na ɗaurin Amren ku , mun kuma gamsu da su , " dan haka baka sau amren matarka ba Youssouf ,  yi aminci ga matarka, ka ƙaunace ta , ka amro ta ne domin kana ƙaunar ta Alhalin kana da damar hakka , kai Mijin mataye ne , "Saboda haka ka yi farin ciki tare da matarka, ka yi murna da budurwa da ka auro, kyakkyawa mai kyan gani kamar barewa , ka bari kyanta ya ɗau hankalinka, daga ɗauke gani bisa matayen banza ,  Bari ƙaunarta ta kewaye ka , daga kwaɗayin macen titi , ƙwarai kana da damar haka ita halaliyar ka ce ,   Wani irin sanyin daɗi ne ya fara tsartuwa a zuciyar Youssouf sai ya ɗago kansa kamar wani soko-soko yana duban Maimartaba da kokonto ko kunnuwansa gaskiya suka jiye masa ?    Ɗorawa Maimartaba yayi da cigaba da cewa ,       " Amma ka tsahirta har abubuwa su dai-daita Mahaifiyarka kuma ta sabko daga fushin ta daga nan sai ka tafi ka zo da matar ka , mafi girman lamari a gaba ka tsaida adalci  a tsakanin Matayen ka babu shakka Allah yana farin-ciki da adalai .    Youssouf a lokacin ji yayi kamar ya tashi ya sungumi Maimartaba ya shiga shilla shi sama yana chafewa saboda tsabar daɗi da zumuɗi ,    " Nagode ranka shi daɗe, Nagode , nagode , nagode  kawai yake ta maimaitawa ,   " Youssouf kada ka manta kalmomin da na furta su gare ka zasu inganta halinka, su zama kayan ado kamar kyakkyawan rawani a kanka, ko kyakkyawan abin wuya a wuyanka, don su ƙara maka kyau ,     "Ban manta ba ranka shi daɗe , Allah shi saka da  Alheri Ranka shi daɗe ,    Gyaɗa kai maimartaba yayi " kana iya tafiya ga iyalin ka .     " to na barka lafiya ranka ya dade mu kwana lafiya .   Da tarin farin-ciki ya nufi sashin sa , da sassarfa ya shiga falon Siyama wacce ta ɗau kwalliya cikin ƙananun kaya riga da siket , jajaye da suka amshi fatar jikin ta mai matsakaicin haske. Da mamakin ganin sa a shiyarta da daren nan , Alhalin kuma yau ɗakin Gimbiya yake kwana , ta miƙe tsaye tana masa sannu da zuwa , Da sassarfa ya taka ya isa gareta ya rungumeta tsam a jikinsa yana shaƙar ƙamshinta mai sanyin daɗi , shafa bayanta ya yi a kunnenta ya ce da ita ,      " ki tayani farin-ciki ƙamnata Maimartaba ya yarda da aurena da Fatima , har ma ya min iznin nan ba da jimawa ba na tai na zo da itta , kwanan nan za ki ga ƙamnar ki . Murmushin yaƙe tayi tana rintse ido , muryar ta da ɗan rawa tace ,    " Alhamdulillah , Madallah da adali mai yawaita Adalci da kyautayi , nayi maka murna Biyamuraɗin maraɗawa ,   Zare jikinta tayi tana ƙin haɗa ido da shi saboda ƙwallar da cika taf a ƙwarmin idanun ta tana daf da kwaranyowa .   " mu tai ka ci abinci   ta ce da shi tana jaan hannuwan sa , Tare suka ƙarasa gaban teburin cin abincin da yake cike taf da kayan cimaka na alfarma . *** Zuwa lokacin Gimbiya Maimounatu ta kai maƙura wajen shaƙar baƙin-ciki , jin ya zo ya yini a gidan bai ko neme ta ba bayan irin laifin da ya aikata mai muni . Ta kasa zama sai kai kawo take , gaba ɗaya yau mummunar zuciyar ta ta ƙeƙeshe ita ke jagorar ta ,    Ko ƙwalliyar da ta saba yi domin taryarsa yau ta gaza , saƙa take da warwara , a ganin ta abunda yayi mata iyaka ne a cin fuska dan haka ta ɗau alwashin cimma manufarta a yau . Duban ta ta mayar ga gnala wacce ita ce ta zo mata da labarin sake shigowar Yarima Youssouf gidan da sake shigar sa sashin Siyama .   Da kaushin murya tace ,    Gnala ,    " na'am gimbiyar matar yari... a tsawace ta katse ta ,     " ki tashi ki tai ga shiyar matar can ki ce ina biɗar ganawa da Major Youssouf  Abdoul-azuzou Youssouf Baskore .   A ɗan firgice Gnala ta ɗago kan ta tana duban uwargijiyar ta , jin yadda yau ta ƙira sunan Yarima garan-gatsau babu wani sakayawa bare girmamawa , sai dai yadda ta ga fuskarta ta tsorata ainun , dan haka ta miƙe jiki na rawa ,ta fice tana cewa ,   "  Allah shi huci ranki Gimbiya ɗiyar Sarki . sanin da tayi bata da ikon shiga sashin Siyama kai tsaye , sai da kamun ƙafar Rakiya shugabar hadiman sashin da ita ce zata yi mata jagora , yasa ta ratsa dogayen bishiyoyi da shuke-shuken farfajiyar gidan ta cimma Rakiya a shiyar ƴan aiki ,   Da kallon banza suke bin junan su , tamkar kishiyoyin da suke zama bala'i,  kamar Mai ciwon haƙori Gnala ta buɗe baki da kyar tace ,    " saƙo dagga Gimbiya tace a shaidawa Matar Yarima , gimbiya na biɗar kaɗaicewa da shi .   Rakiya wacce take cin gyaɗa ƴar marau-marau , ta karkaɗa ƙafa bayan ta afa gƴaɗar ta a baki ,  ba tare da ta dube ta ba tace ,    " kin ga Gnala ki ɗaga sauti kiyi magana yadda zan iya ji amma kin zo kin tsaya akaina kina wani mui-mui da baki ,yo ce miki aka yi aka yi kunnen nawa zuƙo sauti yake ? Aikin banza .   Gnala ta ƙuta , cike da takaicin rashin mutuncin Rakiya. da ƙaƙƙarfan sauti ta ɗaga murya cikin faɗa-faɗa tana maimaitawa mata saƙon Uwargiyar ta ,    " ah ke saurara haka kar ki fasan dodon kunne ki fallasheni , kin zo kina min hargagi akai ya ruɓaɓɓan radi'o ,    " Naji , sai ki wuce mu tafi , tace tana miƙewa ta zira takalman ta ,   Da wani mummunan kallo Gnala ta bita kafin ta dafa mata baya , suna tafe Rakiya na rera waƙar Barmani mai coge "cikin waƙar ɗuwawai ," inda take cewa ,       A hayayye ɗuwaiwai dole a zauna da ku , to ko ana so , to ko ba' a ƙauna ,ko da sun tsiyaye ,  wayyo ladi ko a tsidau , kai koma cikin kwata ne . Daga bakin ƙofa ta nemi iznin shiga wajen Uwargijiyar ta ta hanya matsa mata ƙararrawar dake shaida isowar ta , Siyama wacce ta zuba abinci da zummar fara ciyar da Youssouf sai ta miƙe bayan ta ɗau izni daga wajen sa , fahimta da tayi wani saƙo muhimmi Rakiya take tafe da shi a dai-dai wannan lokacin . Da buɗe ƙofar ta ci karo da Gnala wacce take tsugunne a gaban ta , ba ɓata lokaci ta isar da saƙon Uwargiyar ta .   Murmushi Siyama tayi cikin ran ta tana aiyana " ai shi daman wanzami bai son jarfa ,   Da baya ta dawo tana sanar da Youssouf saƙon Uwargidan sa , jim yayi ," shi ba da gangan yaƙi zuwa wajen nata ba , rigimar ta yake gudu , baya son ta ƙara masa damuwa akan wacce yake ciki ,   Miƙewa yayi tare da yin baya da kujerar dake gaban teburin , tunda har ta sauƙe girman kan ta na ɗiya mace ta ƙira shi , duk kuwa da laifin sa , shi ya zama dole ya tafi gareta ,yayi aikin rarrashi da neman Afuwar ta tunda zuwa yanzu ai yana da ɗan ƙarfin jikin ɗaukar duk wani bore da zata iya yi masa ,   Sai da ya kai tsakiyar falon ya waigo ga Siyama wacce take tsaye jikinta a sanyaye  tana bin sa da kallo , dawowa baya yayi , a hankali ya rungume ta , tsawon wasu daƙiƙai , ya sake ta tare da sumbatar leɓɓan ta a tsanake ,     Daf da fuskar ta , ya kawo tashi fuskar cikin muryar da take tsakanin maƙoshin sa yace ,     " Nagode da kome Ƙamnata , je t'aime pour ça, tu es spécial pour moi seulement ,   Ya saketa a hankali ya juya yana barin falon ,    Tsaye tayi a gurin tana shaƙar ƙamshin sa da yayi saura a gurin , ta lumshe ido tana murmushi kaɗan cikin ran ta farin-ciki ne fal ,      " Da gaske yake da yace yana son ta ? Ita ɗin kuma ta musamman ce a wajen sa ? Ko dai duk farin-cikin kusantar dawowar masoyiyar sa ne ? **** Bayan shigar sa falon Gimbiya Maimounatu wanda yake da rangwamen haske sakamakon ƙasa da aka yi da hasken fitulun falon sosai a tsaye ya hango ta ta juyawa ƙofar baya , A hankali ya taka ya isa inda take tsaye , hannunsa ya sanya ya kewaye cikin ta tare da haɗa bayanta da ƙirjin sa sosai , Da sigar rarrashi yace ,       " Bana cikin Farin-ciki da ganin ɓacin ran ki princesse,  ina bakin-cik... Da wani sauti daban da wanda ta saba yi masa magana da shi ta katse shi ,         "  ya ya kake son samun farin-ciki lokacin da ka kwashi tsawon wasu shekaru kana assasa baƙin-ciki a zuciyar wasu mutanen  ? "  ka baranta da farin-ciki ba zaka yi farin-ciki ba har abada kai ma .     Da ƙarfi ya juyo da ita yana laluben ganin fuskar ta , sai dai hasken wajen ya masa ƙaranci .       " kiyi haƙuri Maimounatu ni ɗin mai laifi ne a wajen ki na sani , Wani ɗan ƙaramin murmushi mai sauti tayi ,     " haƙuri , laifi ?     Ta ce da sigar tambaya , Dariya tayi mai sauti , dai-dai da shigowar ƙira a wayar sa ta cigaba da cewa ,    " Ai ni baka min laifin kome ba kan abunda ka aikata ma rayuwar ka ?  To ma menene dan ka rage dare da yaya ka kuma zo ka amri ƙamna ?  Ai babu wani laifi ga hakan ni dai ta ɓangarena , dan haka kada ka bani haƙuri bisa wannan ba damuwa ta ce ba .   Jiki a sanyaye Youssouf yake bin ta da kallo , sai yake ganin baki ɗaya ta sauya masa ,      Hasken wayarsa ya kunna tare da cewa ,     " Maimounatu meye ya samu fitilun sashin nan ne ? Hala sun mutu ?  Bari za'a sauya wasu ,     " fitilin sashin nan na taya Uwargijiyar su baƙin-ciki ne kamar yadda zuciyata tun-tuni ta kasance a cikin duhun da yake matsananci fiye da wannan , tun a  wata ɓakar-rana cikin ranaku da ka sanya bakin bindigar ka ka tarwatsa min fitilar zuciya ta ,    Wayar sa ya mayar aljihu bayan ya ssnyata a silent , da alama sai yayi da gaske da alama ran Gimbiyar ta shi ya kai ƙololuwa a wajen ɓaci , jin yadda take amfani da wasu kalmomin da ya gaza fahimtar su , Jawo ta yayi ya zauna tare da ita tana bisa cinyar sa ,      "  Duk ki bar waɗannan kalaman Maimounatu , Fatima-zahra ƙaramar yarinya ce , ba zata ƙi ku zauna lafiya ba sann....     katse shi tayi ta hanyar ɗora yatsanta manuni akan laɓɓan sa ,      "shitt , Yarima Youssouf nace kada ka damu ,    Miƙa hannu tayi ta ɗauko tatatcen ruwan 'ya'yan itatuwa da ta sarrafa da hannun ta , ta nufi bakin sa da kofin ,     Jimm yayi yana kallon sheƙin idanunta ta ɗan hasken wajen , dariya tayi yana iya ganin hasken haƙoranta kafin tace da shi     " Sha mana Yarima , abun shan ka ne mafi soyuwa , ni da hannuna nayi sa musamman domin kai .    Ƴar ajiyar zuciya yayi jin alamun ta fara sauƙowa , hannun sa ya ɗora akan nata ya kai kofin zuwa bakin sa , yayi Bismillah ya kafa kai ,     Ya sha sosai saboda ƙishirwar tare da yunwar da ya yini yana ji , ya kuma gagara cin kome sai fa yanzu da ya fara samun nutsuwar zuciya ,     Wata irin damƙa da cikin sa yayi masa kamar kiftawa ido bayan gama sha , shiyasa ya zame Gimbiya maimounatu daga jikinsa ,   Da sauri ya fidda wayar sa daga Aljihu da har lokacin ƙiran Tafeeda bai bar shigowa ba , da hasken shigowar ƙiran ya kai hannu ya ɗau kofin yana haska ciki . Da wata irin muryar yace ,     "Maimounatou menene cikin wannan juives din ?  Meye a ciki ? Meye..  Kasa ƙarasa magana yayi     Gumi ya shiga karyo masa saboda wani irin ciwo mai tsanani da ya ji ya turnuƙe shi tamkar ana filla-filla da kayan cikin sa , zamewa yayi daga kan kujerar bayan ya saki kofin hannunsa zuwa ƙasa ,   Cikin azaba ya ke duban Fuskar ta , yana iya hango wani ɗan guntun murmushin cikar buri da take yi , bata yi motsi ko kaɗan ba wajen ba shi wani taimako     Wani irin gurnanin nishi ya fara yi , ya miƙe a ƙasa yana murƙususu ,ciwon da yake ji bai taɓa jin makamancin sa ba , wani irin duhu mai tsanani yake ji yana sabko masa daga can wani waje mai nisa a kwakwalwarsa Alhalin kunnuwan sa sun samu ƙarin ƙarfin ji ,    Domin yana iya jiyo sautin murmushin laɓɓan Maimounatou , so yake ya buɗe baki yayi ko da addu'a ne amma ya gaza , Wani ciwo mai kaifi da ya yanki uwar hanjin sa shi yasa shi burtso da Amai ta hanci da bakin sa , da yasa duhun da yake sabko masa hanzarin ƙarasa saukowa ya rufe masa ido ya daina ganin kome alhalin idanun sa na buɗe da hakan ya yi dai-dai da tsayuwar jijiyoyin jikinsa , kome kuma ya tsaya masa chak . Da gudu Maimounatou ta tsallake shi tana lalubar wayar ta , jikinta na rawa ta shiga ƙiran wata number ,     Ana ɗaga ƙiran bata jira ance kome ba tace       " ka tahou yanzou aiki ya cika sauran ka ƙarasa naka , ni nagama nawa .   Daga ɗayan ɓangaren Mammadou zuruf ya miƙe tsaye tare da kewaye matar sa ya fita ,      A harabar gidan sa ya tsaya , cikin yin ƙasa da murya yace     " kina nufin yau kin yi nasarar kashe Youssoufa ?   Jin jina kai tayi kafin tace "ƙwarai yau na cimma manufata ta amren sa .                     Assalamu Alaikum masu karatu da fatan kun wayi gari lafiya ? Alherin Allah ya sadu da mu baki ɗaya . Nagode    [12/25/2019, 9:11 AM] +234 706 503 6187: MAFARI ( Hargitsin Rayuwa) Umm'muaz 46 " Yakaka tana nan zuwa ita ma , Ita ce amsar da Falmata ta bawa Maman su , daga nan hira ce ta sarƙe a tsakanin su mai cike da labarin yadda rayuwa ta kasance musu bayan rabuwar su da juna . **** Tiryan-tiryan Falmata ta basu labarin duk wasu bala'o'in da suka afku ga rayuwar su bata ɓoye kome ba illa mummunar rayuwar da Yakaka tayi da har ta kai ga haihuwar Mama da take jin har abada laɓɓan bakin ta baza su taɓa iya bayyana wannan mummunan labarin ga kowa ba .    Ta cigaba da bata labarin ɓacewar Yakaka bayan haihuwar Mama ba tare da ta faɗi ainahin silar barin su da tayi ba har zuwa kan auren su ita da Youssouf yadda kome ya wakana , da rashin lafiyar Mama har zuwa tafiyar su USA da samuwar lafiyar idanun ta , komawar su Niger da kuma dawowar Yakaka , zuwa kan Mutuwar Mama .   Shiru su duka ukun suka yi bayan gama sauraron ta , zuciyar Khaalty Rahima ta girgiza da jin yadda rayuwa tayi walagigi da 'ya'yan ta mata , tsakanin ƙarya da gaskiya , rayuwar rashin gata ta tsantsar wahala abu ɗaya ne mafi ciwo a gareta yadda duk su biyun suka auri Miji guda a wannan ƙarancin shekarun nasu , lalle wannan ƙaddara ce mai girma .   Babu wanda ya fita sanin halayyar 'ya'yan ta duk kuwa da cewa sun jima da rabuwa daga yin rayuwa guri guda , amma ai ita ta haife su dan haka ta san halin kowaccen su tun kafin su mallaki hankalin da zasu iya boye abu a ran su .   Daga zaman Falmata a gabanta kawo yanzu ta fahimci lalle akwai wata damuwa mai girma da take cinta a rai , wanda farin-cikin haɗuwar su bai sa ta manta da damuwar ta ba , ji tayi hankalin yana neman tashi , tana jin kamar akwai wani abu da Falmata take ɓoye mata da tafi danganta shi da Yakaka , dan haka ta muskuɗa tana kallon fuskar ta cike da nazari tace ,   " Falmata kin samu labarin bayyana ta ne kika zo ?  Ko kuma kawai dai kin zo ne ? Murmushin yaƙe tayi kafin tace    " Maman mu ban san kin zo ba , ban San kina nan ba, ta cigaba da cewa Mama ina Yaana da Bulama suke ?  nayi kuka nayi kuka na damu akan sanin ina kike ko kina raye ko kin mutu ?  shekaru suka yi ta tafiya ba tare da mun san halin da kike ciki ba , har na fitar da rai da sake haɗuwar mu a duniya , na koma yi miki addu'a iri ɗaya da wacce nake yiwa Baban mu , kan Allah ya jiƙan ku .    Ƙwallar tausayin ta ya taru a idanun Khaalty Rahima , kafin tace     " Yaana ta rasu a kan hanyar mu ta shigowa maiduguri , Bulama kuma yana nan ya girma , anjima kaɗan ma za ki gan shi ya dawo daga islamiya ,    Ta cigaba da cewa , " Falmata ni na wanke gawar Mahaifin ku a cikin gonar na binne shi , ban yarda gawar mutumin kirki irin sa ta walaƙanta a hannun dabbobin daji ba , bayan na koma neman ku ban same ku ba , na dawo wajen ƙabarin sa mun rayu kwana biyu ni da Yaana da Bulama ina yi ma sa addu'a , kafin mu bar gurin , Allah sarki Mutumin ƙwarai mai tawali'u Allah ya masa Rahama ,    " Amin Mama Amin ,    Falmata ta amsa tana share hawayen da suke zubo mata ,   Amnee ita ta katse musu hirar ganin duk fiye da rabin ta koke-koke suke yi da jimamin rayuwar su da ta wuce .     " Ukhtee Rahima ku bar koke-koken nan haka , Fatima mu tafi ɗaki kiyi wanka ki shirya kafin a kawo miki abinci , "me zaki ci 'ya ta ?   Ɗan murmushi Falmata tayi "kome ma zan ci , amma da zan samu tuwo miyar kuka da man shanu ,     Dariya Amnee tayi tana kama hannun ta " muje kiyi wanka ki shirya , abinda kike so shi zaki ci .   Bayan tayi wanka ta shirya cikin riga da zanen da Amne ta zaɓo mata daga cikin kayan Rahima , tsumu tayi zaune a kujerar gaban madubi ,    " wani irin yanayi take ciki marar kan gado , ga dai ta a gida ta dawo kamar yadda ta zaɓarwa kan ta , take kuma ganin hakan shine zai raba ta da ɓacin-ran da take ciki , daɗin-daɗawa ma ta dawo ta tarar da farin-ciki mafi ɗaukakuwa a wajenta watau haɗuwar ta da Mama , Amma sai farin-cikin nata ya gaza kaiwa ga matakin da take so , baki ɗaya a hagunce take jin zuciya da ƙwaƙwalwar ta sun gaza tsayuwa gu ɗaya bare su taya ta samun gamsasshen farin-cikin da zai wanke mata rai .    Ƙiran sallar La'asar da aka yi , yayi dai-dai da gilmawar tunanin da take ta yunƙurin danne sa tuntuni , wani sashi na zuciyar ta ya tunbuƙo da tambayar ta ƙarfi da yaji ,    " a wanne hali Yakaka da Youssouf suke ciki ? Wataƙila sunyi ta neman ta sun gaji , wataƙila kuma ba su ma wani neme ta ba , dama ce suka samu ta tsara yadda rayuwa zata musu a gaba , ƙila ma ya saki auren ta zuwa yanzu ,   Nan take ta runtse ido Zuciyar ta na tsananta bugu ,    Da sauri ta miƙe ta shiga banɗaki gami da ɗauro Alwalar La'asar , Har ƙarfe huɗu tana kan Sallaya tana addu'o'i domin yaƙi da tunane-tunane , sai da Amnee ta matsa mata ta zo ta ci abinci sannan ta tashi suka koma falon tare , inda suka tarar da Khaalty Rahima ita ma ta idar da sallar ta nan bisa darduma , idanun ta kan falmatan tana duban ta da murmushi irin na zallar farin-ciki ,da ƙauna , ita ma falmatan da murmushi ta tafi a hankali ta zauna a gefen ta , Farantin da aka jera abinci akai amnee ta tura mata gaban ta , " ki cinye duk kin ji ko ? Sama-sama take chakalar abincin duk kuwa da an girka shi yadda take so , miyar ta sha haɗin kayan ƙamshi na gargajiya , ga kuma man shanu gangariya , Sallamar Yakaka da ta sauka a kunnen ta daga bakin ƙofar falon shi yasa ta mayar da lomar da ta ɗauka da nufin kaiwa bakin ta , A hankali ta ɗago kan ta tana ganin shigowar ta ,da kai tsaye Yakaka ita ta doso bata kai ganin ta kan kowa da yake wajen ba , Ganin yadda ta taho yasa Falmata ta tsorata , dan haka ta janye kwanon abincin gaban ta , zuciyar ta na bugawa bata taɓa ganin Yakaka a fusace ya irin haka ba .    Yakaka tana ƙarasowa ta riƙo kafaɗun Falmata da karfi ta jijjigata , muryarta a tsaurare tace ,      " Falmata me yasa kika min haka ? Meyasa kika tafi ki ka barni ? Ashe kinyi girman da za ki iya yin gaban kan ki a rayuwa ? Ashe ni matsayina a wajen ki daman bai wuce na ƴar jagora ba da yanzu kuma lafiya ta samu wajen ki shine kika sanya kan ki a hatsari wajen yin gaban kan ki ? Wallahi da wani abu mummuna ya same ki bazan yafe miki ba Falmata .    Kukan da take riƙewa ya taho mata , sakin kafaɗun ta tayi ta zauna daɓas akan kujerar gefen ta ,  muryar ta cikin kuka ta cigaba da cewa ,      " Falmata kin manta ne da kusancin dake tsakanin mu ? Ashe har akwai wani laifin da ni zan miki ki kasa yafe min ?    Zuwa lokacin ita ma falmatan hawaye ke sauƙa a idanun ta , ganin kukan Yakaka ya karya mata zuciya , a hankali ta zauna a gefen Yakaka , muryar ta na ɗan rawa tace  " Yakaka , kiyi haƙuri ba yadda zan yi ne , kin san... Kawai bazan iya zama bane .   Da wani irin yanayi Yakaka ta ɗago tana kallon ta , baza ki iya zama a gidan auren ki ba saboda ni ko Falmata ? Saboda mummunan kuskuren da na aikata ko ? Saboda...     Da sauri Falmata ta katse ta tana nuno mata inda Khaalty Rahima da Amnee har da Hajja duk suna tsaye suna bin su da kallo ,    "Yakaka kin ga fa Maman mu a tsaye , ga ta nan tana kallon ki , bata mutu ba ,ga Maman mu Yakaka .    A hankali Yakaka ta bi inda take nuna mata da kallo cikin ran ta da ɗarsuwar tunanin ko dai Falmata ta samu jirkituwar tunani ne ? Tunanin ta ya tsaya chak na wasu ƴan daƙiƙoƙi lokacin da idanun ta suka kai kan fuskar Khaalty Rahima wacce take murmushi tana raba ganin ta a tsakanin su biyun cike da nishaɗin sake samun damar ganin su tare a gaban ta . A hankali Yakaka ta mike tana kusantar inda take bayan tsayuwar kukan ta chak , zuciyarta cike da wasi-wasin gaskanta sake ganin ta , sai dai kuma ko a cikin mafarki ta ga Mahaifiyar su ai ba zata gagara gane ta ba ko me kuwa jirkituwar kamanni da ta samu mai-kyau ko mai-muni . Tana ƙarasowa gurinta ta kai hannu a hankali tana tattaɓa jikin Khaalty Rahima, muryar ta a dishe da kukan da tayi tace ,    "Maama ke ce ? Ke ce Mama ?    Hannun ta da yake taɓa jikinta khaalty Rahima ta riƙe , tana cewa , "Ni ce Aminatu , Yakaka na , ni ce ,   Yakaka tana wata ƴar Dariya-dariya , kuka-kukan da yake fallasa tsantsar ruɗanin farin-cikin da take ciki , ta waigo ga Falmata tana mai mancewa da Falmatan ta riga ta haɗuwa da Mama , ɓakin-cikin da ta shigo da shi yana zagwanyewa tace ,     "Falmata wallahi Maman mu ce , kin ga Maman mu ? Zo ki gan ta , ta ƙarasa magana tare da yafito Falmatan da hannu ,    Sai kuma ta juya ta rungume ta da ƙarfi tana cewa ,"Mama na, Alhamdulillah , Alhamdulillahi . **** Daren ranar ba suyi wani baccin kirki ba su duk huɗun hira kawai suke yi inda cikin labarin da Yakaka ta basu ta bayyana musu ainahin yadda haɗuwar ta da Youssouf ya kasance da yadda ta haifi Mama , samy baby ta yaudare ta, da kuma duk abubuwan da suka kasance tsakanin ita da Youssouf da danginsa baki ɗaya bayan zuwan ta Niger har zuwa guduwar da Falmata tayi ta bar ta a Niger . A Zuciyar ta ta ƙudiri aniyar tsage gaskiya kome ɗacin ta , ita bata ga Alfanun ƙarya ba , babu wata rana da ƙarya zata iya yiwa mutum illa sada shi da ranar Nadama . Daga Khaalty Rahima har Amnee sun koka kan yadda mummunar kaddara ta faɗawa Yakaka sanadin duhun jahilci tare da zun-zurutun rashin wayo , haɗi da raunin wayewar mu'amalantar jama'ah , da kuma rashin wani babba majiɓanci a cikin rayuwar su . Yadda zuciyar Yakaka ta cika da tsoron ko zasu yi mata faɗa ko ma su yi fushi da ita sai ta ga akasin haka , domin daga mamar su har Amnee tausayi kaɗai take iya hangowa a fuskokin su , dan haka sai ta ji ta samu nutsuwar zuciya irin wanda bata taɓa samu ba tunda igiyar rayuwa ta fara jan ta .   A gareta yau ce rana ta farko da wasu nata makusanta na haƙiƙa suka fahimce ta ba tare da sun ƙalubalance ta ba , babu shakka babu kamar uwa Mahaifiya, ƙaunar ta ga abunda ta haifa daban ne , haka ma yawan sani da fahimtar ta ga 'ya'yan ta daban ne kamar yadda yawan uzuri da afuwar ta gare su ya hauhauwa .    Amnee ita ta katse shirun tsakanin su inda ta cigaba da cewa ,     "Amma takwarata , raba auren ƙanwar ki da Youssouf da kika so yi , ko kusa ba hanyar samar da mafita ba ce ba , idan kika duba yadda sharri ya biyo ta hannun sa haka nan ma Alkhairi ya zo ta hannun nasa , ki duba yadda ya riƙe auren ƙanwar ki har ma ya zama hanyar samar da lafiya a gare ta ? Bai walaƙanta ta ba duk kuwa da tazarar banbancin matakan matsayi ta kowacce fuska na rayuwa da yake tsakanin su , Baki ga yadda ya jajirce kan rayuwar ƴar sa ba har sai da Allah ya ɗauke ran ta ba tare da ya bari ta walaƙanta ba , kamar yadda sauran mafi akasarin ƴaƴan da aka samar ta wannan hanyar suke rasa tudun-dafawa iyayensu duk biyu na kƴamatar su musamman ma uba , amma sai shi ya kasance mai bata kariya da dukkanin ƙarfin sa , hatta a gaban dangi da Al'ummar sa . "Babu shakka laifin sa maigirma ne sannan alkhairin sa kuma mai yawa ne , na fahimci irin ciwon da kika ji , kike kuma kan ji bisa dalilin faruwar kome , ina nufin auren sa da Fatima , to amma kiyi haƙuri ki rungumi kaddarar ki , ki yafe masa domin 'yar uwar ki da ya alkintawa rayuwa , ki bari su cigaba da zaman su na aure , Ubangiji Allah zai dube ki kema takwara zai baki Miji nagari wanda zai tallafawa rayuwar ki , ya rufe duk wani aibunki , ya ƙi duba zuwa duk wasu shuɗaɗɗun laifukan ki , ya zamar miki abun Alfahari , Allah yana son bayun sa masu yawan yafiya kin ji ko ? Ta ɗago kan ta a hankali tana murmushin da iyakar sa bisa siraran laɓɓan ta , idanun ta na sheƙin hawayen da suka cika gurbin su ta ce , "Amnee nagode , nagode da addu'ar da ki ka min , kuma inshaAllah na yafe masa Allah ya yafe min nima ,    Hannu ta kai ta riƙo hannun Falmata wacce tayi lamo a kwance kusa da Mamar su , ta juya musu bayan ta , duk zaman su a ɗakin bata cika cewa kome ba , a sarari damuwa mai-yawa take bayyane a fuskar ta ,      Cikin sanyin murya Yakaka tace ,     " Falmata ke ma ki yafe min duk wasu laifukan da nayi miki da saka ki a damuwa da tashin hankalin da nayi , ki yi haƙuri kin ji ko ? ban yi da gangan ba .     Miƙewa zaune  tayi tana riƙo hannuwan Yakaka duk biyu , muryar ta na rawa ta ce ,    "Yakaka meyasa za ki bani haƙuri ? Bayan ke kika cike min gurbin Mahaifiya , Mahaifi ,dangin da kowa namu lokacin da muka rasa kowa ?Bayan ke ce kika dunga ɗawainiya dani Alhalin ina musaƙa ? Ke ce kike zama da yunwa domin ni naci , ke ce kika sadauƙar da rayuwa ƙarƙashin rufin ɗaki kan katifa kika zaɓi kwanan cikin zaure domin ni na kwanta ? Yakaka, ke ce fa Mamar Mama 'yar da dalilin ki samar muna da rayuwar jin daɗi kaddara ta sa aka samar da ita , 'yar da ni kuma ban so wata halitta sama da ita ba , dalilin Mama na samu lafiyar idanuna , tsawon zamana da shi Albarkacin Mama nake ci ,...   Hannu Yakaka ta kai da nufin rufe mata baki , " ya isa Falmata ki ce kawai kin yafe min nima ,    Janye hannun Yakaka tayi daga kan bakin ta hawayen idanun ta da suka taru suna zubowa tace ,     " Yakaka ai ni ce zan nemi yafiyar ki akan butulcin da nayi miki , shaiɗan ne ya min huɗuba da har ya sa nayi fushi da ke , ruɗewa nayi Yakaka ban taɓa zaton abinda ya cutar da ke ni kuma zai kyautata min ba , ban yi zaton sanadiyyar shan wahalar ki ni zan samu salama ba , ban so ba kika zamto mafarauciya ni kuma cima-zaune ba , Yakaka nima bazan iya cigaba da zama da shi ba ..     Kuka ya ci ƙarfin ta , zuciyar ta na mata zogi , Yakaka ma hawayen take yi a dai-dai lokacin bata da sauran kalmar da zata yi amfani da ita ta rarrashi Falmata , ta ta zuciyar ma jinya take . **** Washe gari da safe bayan sun shirya sun yi karin-kumallo Amnee ta musu jagora zuwa wajen Prof da daman tun a jiya labarin zuwan su ya same shi , haɗi da dangantakar su da Amnee da Rahima . Bayan ya amsa gaisuwar su , ya dunga bin su da kallo cike da tausayi , can daga ƙasan ran sa yana jin tamkar yana da kamasho mai yawa na kasancewar rayuwar su a haka , Ba domin shi da danginsa da suka ƙi auren  Rahima da ɗan uwan su ba da hakan ya kawo barin Rahimar gidan da wataƙila yaran basu tashi 'ya'yan ƙauye marasa galihu irin haka ba , Da ace ko da mahaifiyar su da sauran 'yan uwan su sun ƙi auren , shi bai biye musu wajen nuna tsanar lamarin ba da har ya kawo saɓani tsakanin sa da Matar sa ba , ya tsayawa Rahimar har ta samu wani mijin ko da ba ɗan uwansa ba , da Rahima da yaranta basu sha wahalar rayuwa irin haka ba , da suka faɗawa hatsararruka da dama mafi munin su hatsarin Ƴan tawayen Boko Haram , da ko babu kome mutumin birni zai aura mata mai daraja da ƙima kamar ta sa . Yana jin yanzu lokaci ne yayi da zai gyara kuskuren sa , har yanzu yana da damar sake zaɓowa Rahima wani mijin muddin ta amince , 'ya'yan ta kuwa daman Allah ya faɗo da taimakon su ta hannun sa , ashe akwai abunda Ubangiji ya ɓoye , Dan haka ƙudirin haɗin Auren Hamza da Yakaka da ya yi niyyar yi tuntuni ya ji ya sake kaurara a cikin ran sa , har ma ya ji dacewar matso da lamarin kusa , wataƙila da jajircewar da zai yi cikin Rayuwar Rahima da 'ya'yan ta a sauran rayuwar da ta yi masa saura zai samu ya ragewa kan sa girman laifin da yayi wajen tayawa a wargaza rayuwar Marainiyar yarinyar da take amana a wajen sa . Cike da nuna tsantsar kulawa ya shiga jan su da hira ba tare da ya shigo musu da wata tambayar da ta shafi ɓangare na rayuwar su ba , cikin hirar da kusan su biyun ke yin ta a tsakanin su Amnee tace ,     " Baa Alaji , a ƙira yaran nan duk a sanar da su dawowar ƴan uwan su , saboda a sa rana su zo su gana da juna ko kuwa ?   " Hakane , to amma tun da daman nan da ƙasa da sati huɗu ya rage bikin ita Rahima ƙarama kuma a halin yanzu ita da Zainab ɗin duk basa ƙasar suna can Dubai ko da an sanar da su dawowar ƴan uwan nasu sai a bar batun haɗuwar su har zuwa nan da sati biyu da duk zasu hallaru domin bikin Rahima .     " to shikenan Baa Alaji bari yanzu zan ƙira idan mun koma ciki idan ma ya kama a haɗa su a waya su fara gaisawa ,    " to babu laifi , ya zarce da cigaba da cewa,      " Rahima baku da wata damuwa ko ? Da sauri Khaalty Rahima ta amsa ,   " babu damuwar kome Yaya , Allah ya saka da Alheri ya ƙara nisan kwana .   Amin yace yana Gyaɗa kai ya mayar da ganin sa kan su Yakaka ,      " Yarana kuma babu wacce take da wata matsala ko ,? Idan kuna da ita ku sanar da ni , ni tamkar Mahaifi nake a wajen ku Mahaifiyar ku ƙanwata ce ,    Girgiza kai Yakaka tayi , a hankali tace "Baa babu matsalar kome mun gode , Falmata wacce kan ta yake sunkuye ta ɗago kai kamar zata yi magana sai kuma tayi shiru tana sake sunkui da kai ,    Prof da duk yake kallon su yace ,   "Fatima akwai matsala ko ? Meye kike son ki faɗa min , ina jinki ƙaramar 'yata ?   Dukkanin su sai suka mayar da ganin su kan Falmata wacce kan ta ke sunkuye ,   'Baa so nake Dan Allah ka raba auren mu , bana son cigaba da zama da shi ko kaɗan Dan Allah Baa ka sa ya sake ni .    Muryar Falmata ta ratsa wajen cikin alamun da take gaf da fashewa da kuka , Shiru ne ya ratsa falon , tamkar ruwa ya cinye su , kafin Prof yayi gyaran murya yana karantar yanayin ta yace ,    "Fatima shi mijin naki laifi ya yi miki ? Ko kuwa wani abu aka miki daga danginsa ? Ko kun samu saɓani ne da shi ?   Shiru tayi bata amsa ba , sake maimaita mata tambayar yayi nan ma tayi shiru , Khaalty Rahima zata yi magana ya dakatar da ita ,    Ya sake cewa    "ko kuwa kawai daina son shi kika yi ? Ko gajiya da zaman ku tare kika yi  ? Ko kuma can ƙasar tasu ce bakya so ?   Da sauri ta gyaɗa kai , murmushi mai sauti yayi , cike da tausasawa yace " to babu laifi , ki ƙira shi kice na ce ya zo ina son ganin shi , idan ya zo sai a yi miki yadda kike so kin ji ko ? " to Baa nagode . Murmushi yayi bai ce ƙala ba .     **** Niamey Police nationale Maimounatou wacce take zaune daga kan wani ɗan dandamali da aka tanada shi musamman domin zaman waɗanda ake tuhuma da laifi a cikin babban ofishin 'yan Sanda na ƙasar Niger baki ɗaya . Ta muskuɗa tana cigaba da wasa da awarwaron hannun ta , tayi kunnen uwar shegu da duk wasu manya da ƙananun tambayoyin da babban ɗan Sanda da yake tsaye daga kan ta yana jefo ma ta , Ganin taƙi yin magana ya sa ɗan Sandan ƙutawa cike da kaiwa maƙura a jin haushin ta , ya mayar da ganin sa kan Mammadou bayan ya ɗaga takun sa zuwa gaban sa ,    " Mammadou ko za ka iya faɗa mana dalilin da yasa ku ka ciyar da ɗan ouwan ka guba ?      Da sauri Mammadou ya ɗago da kansa ,    " Wallahi ni bani da wata masani kan abunda yake faruwa a shiyar gidan Youssouf , matar sa ita tayi ƙira na kan cewa na zo fa ga ɗan ouwana ya faɗi yana biɗar taimako na , shine na runtuma da niyyar kai masa ɗauki , da shigata na tadda shi a halin da ku ma kun ka zo ku ka taddo shi , wallahi ni iyakar abunda na shina kenan ban..... Wata dariyar mai sauti da Maimounatu ta sanya , ita ta katse masa jawabin sa ya mayar da ganin sa kan ta yana ƙif-ƙifta ido , ba tare da ta dube shi ba tace    " Mammadou wallashi cikkin ragwaye kai na ƙurya ne , yo me kake tsoro idan ya tabbata gubar da shi wannan Azzalumin ya ci ta hannun ka ta fitto ? hukuncin kisa ta hanyar rataya ko kouwa ɗaurin rai da rai muddin rayuwa ?      " Burina labarin mutuwar sa ta jishe ni , daga nan koume shi faru dai-dai ne , ai hukuncin wadda ya kashe a kar shi , shi da kansa bisa turba nasa hukuncin yake , fansar ran Ghaddafi tare da gudan jina na da na rasa na ɗauka bissa kan sa , kai gudumawa ka bada bisa turbar naka cikar buri ko kouwa ?      Laɓɓan bakin Mammadou har rawa suke cikin in'ina yace ,     " kadda ki mini ɓakin sharri ɗiyar nan , ni yaushe na kawo miki gubar da kika ciyar da ɗan ouwa na da itta ? Ki yiwa Allah kadda ki tunkuɗa ni cikin masifa ,    Wani kallon banza Maimounatou ta wurga masa , idanun ta jajir tace .     " Yau ba rana ce ta yin wassan ƴar boye ba Mammadou ka daina yin kamar baka san kome ba , kamar kai da Mahaifiyar ka baku taya ni ba , bana son muyi rabuwar tsiya doumin kun bani taimako wajen biya hakkin Ghaddafi tukuici ya kamata na baku .    Ɗan sanda da yake rubuta duk wasu kalamai da suke yi , ya ɗan karkato ga Maimounatou , ganin kamar ta shirya bada wasu bayanai ,        " Wanene Ghaddafi menene kouma alaƙar sa da kashe Mijin ki da kika yi ta hanyar ciyar da shi guba .   " Ghaddafi masoyina ne . **** Ghaddafi Yacouba Dango asalin iyayen sa ƴan ƙasar Mali ne da suka hauro sahara suka shigo ƙasar Niger , suka yada zango a yankin Agades , inda suka yi mazauni cikin wani kongon gida da yake daga baya sosai da Babban gidan sarkin Agades ( fadar Maimartaba sarkin Agades ) . Bayan shi iyayensa suna da wasu 'ya'yan sai dai tsantsar talauci ya sanya su fantsama a cikin gari yin barace-barace , duk kuwa da cewa a lokacin shi Ghaddafi saurayi ne mai kimanin shekaru ashirin da ɗoriya , Lokacin da ya fara bara sai ya fahimci babu mai kula shi bare har a ba shi , dayawa daga cikin mutanen da yake roƙo ma ƙorar sa suke da zagi kowa na faɗin ya tafi ya nemi sana'a . Ganin haka ya sanya shi daina bara ya koma tsince-tsincen matattun ƙarafuna a kan bola yana kaiwa yana sayarwa ,( jari bola ) babu laifi yana tallafawa iyayen sa da hakan . a wannan yawon ya haɗu da wasu kangararrun yara sa'o'in sa da suke jeruwa bisa tsohon hanyar wucewar jirgin ƙasa wajen da aka mayar sa bola su kuma suka mayar da shi matattarar ƙananun shaye-shayen su da yin karta . Su suka jawo sa cikin su ba ɗau lokaci ba ya zama ɗaya daga cikin su ya kangare , tsince-tsincen ƙarafunan ma ya daina ,  basu da wani aikin yi sai zaman banza a bakin layin jirgi ko kan katagun kwangayen gidaje , suna ƴan shaye-shayen su ,  babbar sana'ar su ita ce ƙananun sace-sace , daga sun ga gidan da ake barin sa galala sai su faɗa su yashe mutanen cikin sa , ƴan ƙananun dabbobin mutanen unguwa basu tsira ba , akuyoyi ,talo-talo kaji , agwagi , a taƙaice dai su Ghaddafi sun addabi mutane sun hana su sakewa .   Ganin haka yasa Mutane suka yi ɗango suka kai ƙarar su wajen Maimartaba , Da kansa Maimartaba ya sa aka kamo su , aka basu horo tare da haɗa su da aiyuka a cikin gidan sarkin mai wahalarwa na tsawon satika biyu duk saboda a hora su  Ghaddafi yana cikin samari huɗun da aka tura bargar dawakai domin kula da su da share musu waje gami da basu abinci . Kafin kwanaki huɗu Ghaddafi ya saba da aikin yana kuma jin daɗin aikin saboda ko babu kome yana ci ya ƙoshi fiye da sau uku a rana Ranar da yake cika sati a kan aikin sa , Babban bawan da ainahin kula da bargar yake ƙarƙashin sa ,  ya danƙa masa linzamin wani kyakkyawan matashin jan doki , Yace ya kaɗe jikin sa da kyau dokin gimbiya ne , yau zata ɗan hau ta kewa akan sa nan cikin filin dake gaban bargar . Zuwa la'asar sakaliya , gimbiya Maimounatou tare da bayunta biyu suka iso Ba ɓata lokaci ya jaa limzamin dokin zuwa gaban ta yana mai tsare ta da kallo ganin ta da yayi yarinya ƙarama da bata wuce sa'ar ƙanwar sa ta uku ba , Gimbiya Maimounatou tana ɗago kai ta sauke ganin ta a kan sa , zuciyar ta ta wani irin bugawa , a iyakar shekarun ta goma sha shidda alokacin bata taɓa ganin wani ɗa Namiji mai kyaun sura irin sa ba , kasancewar Ghaddafi kyakkyawan balarabe ne na sosai jazur da shi . Tun daga wannan lokacin sai ta faɗa jarabar ƙaunar sa , bata da aiki sai zuwa barga dan kawai ta kalle shi , a lokacin ita tana hutun kammala makarantar ta ta secondry , Sai dai kamar ɗaukewar ruwan sama sai ta rabu da sake ganin sa bayan wasu ƴan kwanaki , duk yadda ta so ta daure ta manta da shi , ta gagara a hankali damuwar rashin cigaba da ganin sa ta fara duƙushe walwalar ta , saboda wannan ne karo na farko da zuciyar ta ta fara son wani ɗa namiji , Ganin damuwar ta na neman kai ta ƙasa , sai ta nemi Gnala da ta bincika mata wanene wannan sabon balaraben bawa ? me kuma yasa ta daina ganin sa ? Ko an sauya masa shiyar aiki ne ? Ba'a ɗauki wasu kwanaki ba ta samu duk wasu bayanai game da Ghaddafi , sunan sa , asalin sa , iyayen sa da laifin da suka yi har aka kawo ƙarar su ga Maimartaba aka hukunta su . Kuka ta zauna tana yi sosai , so take ta tunbuƙe son shi daga ran ta ji da tayi ko kusa basu dace da juna ba , shi ɗin maƙasƙanci ne ko a cikin maƙasƙanta ko ɗaya ba shi da nagarta da ya dace da samun soyayyar ta . To sai dai ita zuciyar da so na farko ya fara fasawa ya dasu a cikin ta tauri ne da ita tare da ƙwalafaci , dan haka bayan wasu kwanaki kaɗan sai ciwon son shi ya dawo mata sabo fil , Jin ba zata jure rashin ganin sa ba yasa bayan ta samu tabbacin inda yake zama da la'asar sai kawai tayi badda-kama cikin baƙaƙen kayan su na buzaye ta rufe rabin fuskar ta da mayafin ta , ta ratsa sorayen gidan su ba tare da ta bari kowa ya gane ta ba ta fice daga gidan su rana tana daf da faɗuwa , bata ko damu da iskar hunturu wacce ke tayar da rai-rayi da take ta busawa tana tila ƙasa a idanu hanci har ma da kunnuwan al'umma ba , Kasantuwar bata saba fita ita kaɗai ba hasalima yau ce rana ta farko da ta taɓa tako ƙafafun ta shiyar unguwar da take baya da Masarautar su da take ta talakawan liƙis , sai tayi ɓatan kai , ta gagara gane kwatancen da Gnala ta yi na inda aka ce Ghaddafi yana zama , ta nemi hanyar jirgin ƙasa ta rasa . Ƙura tayi buɗu-buɗu da baƙaken kayan jikin ta , magariba kuma ta kawo kai , da kyar ta samu ta tsayar da wata budurwa ta tambaye ta ina ne tsohon hanyar jirgin ƙasa ? Budurwar ta gwada mata hanyar da hannu, juyawa tayi da sauri ba tare da ta ko yi mata godiya ba ta fara taku zuwa kan hanyar da ta mata nuni ,   " hala can kike noufin zouwa ? Ko kouwa kin san da kwai hatsari bissa hanyar kou ? Kin san fa an sau waɗannan tsinananan samari da suke ratse bissa hanya nan , a shawarce kadda ki bi ta wannan hanyar war hakka .    Tsayawa tayi cak , ba ta juyo bata kuma ce ƙala ba , sai ta sake kaɗa kan ta tayi gaba ta miƙa sosai a hanyar har ta tarar da matattciyar hanyar jirgin ƙasan da duk bola ta mamaye ta , Warin da yake wajen ya sanyata rufe hancin ta tana tsallaka tsumi-tsumin bolar da take wajen , Shal hanyar take babu kowa ko ƴan dabbobin da suke kiwo akan bolar babu kowa ya kaɗa dabbar sa gida kafin a sibare masa ita gobe kasuwa . Sai hange-hange take yi cike da burin son ganin sa , Taku ta fara ji daga bayan ta kafin warin taba ya mamaye ƙofofin hancin ta , Da sauri ta juyo karaf suka haɗa ido da shi tare da waɗansu samari biyu daga dama da hagun sa , Daga cikin mayafin ta ta saki tattausan murmushi zuciyar ta na cika da farin-cikin sake ganin sa , Warware mayafin fuskar ta tayi , ranar da tayi jazur gaf da faɗuwa ta haske ta tana ƙarawa farar fuskar ta jaa da kyau , cikin siririyar muryar ta tace " Ghaddafi wajen ka na taho . Zaro ido yayi yana daɗa kallon ta , babu shakka wannan gimbiyar nan ce ɗiyar sarki to me ya kawo ta wajen nan me kuma take nema a wajen sa ?? Hayaƙin tabar da ya cika bakin sa da ita ya fesar ta hanci ta baki . Tun bayan wannan ranar sai soyayya mai ƙarfi ta ƙullu tsakanin ƙananan matasan biyu ba tare da tunanin me ke je ya dawo ba , soyayyar junan su ta rufe musu ido daga hango tarin banbancin dake tsakanin su , Cikin watanni shidda sun yi wata irin shaƙuwa ta ban mamaki duk kuwa da cewa daga ɓangaren ita Gimbiya maimounatou babu wanda yasan da batun soyayyar su ita da Ghaddafi  , sau biyu kawai suka taɓa haɗuwa , rana ta farko da ta je wajen sa sai kuma rana ta biyu da ta kai masa kyautar wayar tafi da gidanka sabuwa dal , da ta sa Mahaifiyar ta ta saya mata lokacin ma wayar sai hannun wane-da-wane tare da wasu kuɗaɗe masu yawa . Zancen tafiyar ta makarantar jami'a ta babbar birnin Niamey shine ya tayar da hankalin su , saboda nisa da zasu yi da juna . A gobe zata tafi makaranta , ta saci jiki kamar yadda ta saba ta je wajen sa da hantsi , Akan ƴar rusasshiyar katangar wani kangon gida ta tarar da shi , a shirye tsaf yake cikin wandon gonjo da rigar sanyi mai haɗe da hula da ya saya daga cikin kuɗin da ta masa kyautar su . Yana daga sama yayi mata nuni da gefen sa kan katangar akan ta hauro ta zauna , Dariya tayi da haƙoranta tana kaɗa kai tace     " Bani iya hawa bissa nan ai kaima ka sani , Murmushi yayi ya diro ƙasa bata ankara ba ya ɗaga ta ya ɗora ta kan katangar runtse ido tayi zuciyar ta cike da tsoro , Bata san zaman sa a gefen ta ba sai da ya zunguri kafaɗar ta , a hankali ta wara ido tana kallon sa , sam ta kasa sabo da takaɗarancin Ghaddafi ita bata saba irin wannan rayuwar ta ƙarancin tarbiyya ba .    Cikin muryar sa mai sanyi sosai ba'a ce daga bakin sa amon ta ke tasowa ba yace ,      " ranki shi daɗe ai bashi kamata ba ke kina ƙasa ni ina sama tsololo , ke ai gimbiya ce ɗiyar sarki ni tamkar bawa nake a gare ki ,    Hararar sa tayi sai kuma tayi murmushi , a hankali tace    " bana so kana taɓa min jikina , kuma kai baka cikin jerun bayun gangar jikina amma zan yi farin ciki da zaka zama bawan zuciyata .     Murmushi yayi mai sauti , " ai tun-tuni nake hadimi ga zuciyar ki gimbiyata , amma meyasa bakya son ina taɓa ki ? Ya tambaye ta yana kallon gefen fuskar ta    " kawai ba yanzou ba , ta bashi amsa " sai yaushe ,  yace yana shilla ƙafar sa    " sai mun yi amre kou ? Ta ce tana rufe fuskar ta da tafukan hannun ta duk biyu .   Ganin sa ya dawo kan ta , kafin ya ɗauke kan sa zuwa sama kaɗan da wata muryar dake bayyana ciwon zuci yace    " Maimounatou bani da matsayi , nagarta  , kyaun asali kou dukiyar amren ki , ke ɗin kouma ai shaida ce bisa hakka . Ganin ta ta mayar kan sa , tana jin yanayin ta na nishaɗi na jirkituwa zuwa tashin hankali da damuwa tace ,   " Amma ai muna ƙamnar juna , abunda ka lissafa bai issa hana amren mou ba , tunda ai zaka iya sauya halaye sannan kouma kai Namiji ne kana da ƙarfi neman dukiya ko baka iya zage damtse wajen neman dukiyar amre na ?   Idanun sa da suka fara yin jaa ya nitsar cikin nata raunanan idanun ,   "  ta wacce hanya zan nemi dukiyar amren ki maimounatou baya.....    Katse shi tayi jin yana shirin ɓata mata walwalar ta ta yau baki ɗaya alhalin kuma bankwana ta zo su yi , tace da shi    " ka nemi dukiyar Amren Maimounatou ko ta wacce hanya Ghaddafi , buƙatata kawai muyi aure dagga na kammala ecole . **** Bayan tafiyar Maimounatou sun cigaba da kasancewa a waya ita da Ghaddafi suna sake cinye zuciyoyin juna da so da ƙaunar juna , Basu sake haɗuwa ba sai bayan shekara guda a ranar da take ta zagayowar haihuwar Maimounatou , Babu zato aka sanar mata da sakon ƙiran da wani baƙo ke yi mata a can filin makaranta , tayi mamaki sosai saboda duk cikar jami'ar babu wani ɗa namiji ɗaya da suke ko da gaisuwar kirki ne . Amma haka kawai ta ji zuciyar ta na son zuwa amsa ƙiran koma wanene , dan haka ta kama hanyar inda aka kwatanta mata A tsaye ta tarar da mai ƙiran nata ya bada baya a jikin wata ƴar ƙaramar mota ƙirar golf da ta sha jaan fenti tana ta ɗaukar ido . Daga sama har ƙasa take kallon sa zuciyar ta na kai-kawo wajen tantance shi ɗin ne ko ba shi bane ? Juyowar da yayi ya hutatshe da zuciyar ta daga tunanin tantance shi , saɓanin haka zallar farin ciki ta ji yana tunbuƙowa daga ƙasan ranta , tamkar tayi tsalle ta rungume shi take ji a lokacin    Hannunta biyu ta kai tana rufe bakin ta da haƙoranta ke buɗe tana dariya , sai kuma tayi ɗan tsalle tana matsawa daf da shi ta haɗo haruffan sunan sa cikin wani irin sauti mai nuni da ɗoki da farin-ciki da take ciki tace.       " Gha°ddafi ? Kai ne ? je ne peux pas croire mes yeux mon amour ,    Dariya yake lokacin da ya zare baƙin tabarau ɗin dake idanun sa , cike da murnar ganin ta ya kai hannu ya riƙo hannuwanta ya jaa ta yana ƙarasa rufe tazarar dake tsakanin su ya haɗa ta da jikin sa , cike da salon son ya burge ta ya harhaɗo kalmomin da ya shafe tsawon wata guda yana koyon su yace ,      " tu m'as tellement manqué chérie , Bayan sun gama ɗokin ganin juna , Maimounatou ta kasa ɗauke idanun ta daga kan sa duk wani motsin sa ƙara burge ta yake yana sake nutsar da ita cikin ƙaunar sa , Yadda yayi shar da shi yayi gayu ya sake fiddo tsantsar kyaun sa , da cikar zatin sa na matashin Namiji , kasa jurewa tayi ta tambaye shi ,     " Ghaddafi ina ne ka samou dukiya hakka mai yawa har ka sai moto ta hawa , ka gan ka kouwa yadda kayi gayu tamkar ɗiyan saraki wallahi ka burge ainun ,   Ƴar dariya yayi ,kafin yace da ita    " cikin dukiyar amren mu da na fara taru na ɗauki kaɗan na sayi suturu doumin nayi kwalliya na burge ki , kadda samarin jami'a ƴan gayu su kwace min ke , Ba tare da ta damu da ta tambaye shi wacce sana'a ya fara yi ba ta washe ƙaramin bakin ta tana cewa    " Duk faɗin babban birnin Niamey babu namijin da zai iya kwace maka ni Ghaddafi ,   Da murmushi a fuskar sa ya buɗe kujerar motar sa na baya ya shiga fiddo manyan kwalayen da yayi mata birthday gift yana jera mata a gaban ta , Zuciyar ta tana sake bunƙasa da ƙaunar sa take bin sa da kallo bata ƙi ba ace cikin wata mai kamawa a ɗaura auren su . ***** Cikin shekaru huɗu na karatun ta Ghaddafi ya bunƙasa ya zama hamshaƙin attajiri , ya ma ɗauke iyayen sa da ƙannen sa daga Niger ya mayar da su can ƙasar su Mali ya gina musu sabuwar rayuwa ya ƙere musu gida na zamani . Zuwa lokacin ita da kan ta Maimounatou tasan Ghaddafin ta ya sha kwana , ana kuma damawa da shi a harkokin masu dukiya , sai dai ita da kan ta ba zata ce ga takamaimai sana'ar sa ko aikin sa ba , baza ta ce ga inda yake samun kuɗaɗen da yake mata wasa da su cikin kyautuka na bajinta ba da har wasu lokutan takan yi masa faɗan kuɗaɗen sun yi yawa , amsar da kullum yake bata shine        " wannan kaɗan ne dagga cikin dukiyar Amren ki da nake biɗa ina tarawa Maimounatou, Soyayyar su kuwa sai abunda yayi gaba kusan kowa da yasan Maimounatou yasan da soyayyar ta ga Ghaddafin ta , idan aka cire iyayen ta amma hatta ƴan uwanta makusanta kowa ya san sunan sa , sun kuma shaida wasu daga cikin manyan kyautukan da yake yi mata , Haka shi ma ta ɓangaren Ghaddafi tun daga kan iyayen sa da ƴan uwa zuwa abokanan sa tun na farko da suka riga daman suka san da Gimbiya Maimounatou har zuwa kan sabbin abokan sa babu wanda bai san labarin Gimbiya Maimounatou ba , A cikin shekarar ne kuma gwamnatin ƙasar Niger tayi hoɓɓasa kan gagararrun ƴan fashi da makamin da suka addabi baki ɗayan kusurwowin ƙasar ta Niger ta kan kowacce boda guda bakwai da kasar ke da su ta Nigeria, Chad, Algeria, Mali, Burkina Faso, Libya, da Benin. sun hana duk wani ɗan kasuwa shan ruwa ya tsirga masa cikin ƙasa da shekaru biyar , da har suna ne da su na musamman da ake ƙiran su da shi escouade de lions . escouade de lions sun gagari kananun sojoji su waye kuma ƴan sanda ? bare kuma ma'aikatan hana safara da miyagun kaya ,  ƙananan ƙwari a wajen su kenan , Kisa suke tare da ɓarna yadda suka so suka ga dama , gwamnati ta rasa yadda zata yi da su , dayawa daga cikin su ɓoyayyun fuska ne da su babu takamaimai wanda ya san fuskokin su , sannan an gaza gano takamaimai madakatar su da za'a iya taƙile su ta nan . Youssouf Abdoul-Azizou Baskore ,shine sojan da babban hafsin soja na ƙasar Niger ya wakilta a matsayin wanda zai ja tawagar aikin da zai kawo ƙarshen waɗannan gungun ƴan fashi da makamin , lokaci kaɗan bayan dawowar sa daga ƴakin da aka tura su Libya. Cike da zuciyar jarumta da son kare hakkin ƴan ƙasar sa Youssouf ya karbi aikin da aka ba shi , inda ya nemi taimakon haɗin guiwar ƴan sandan ciki da dole sai da taimakon su za'a kai ma nasarar cafke ƴan fashi da makamin . A dai-dai lokacin rayuwa ta yiwa Ghaddafi da Maimounatou daɗi domin watanni uku kaɗai ya rage mata ta kammala karatu baki ɗaya ta bar makaranta , abu na gaba shine ta gabatar da Ghaddafi ga iyayen ta , a ɗaura musu aure daga nan su shilla zuwa ƙasar France da suka zaɓe ta a matsayin kasar da zasu barji amarcin su a can. Kafin cikar watannin wani irin liƙewa Ghaddafi ya yiwa Maimounatou koyaushe yana sintiri tsakanin garin da yake da Niamey , Duk da cewa Maimounatou tana jin daɗin yadda yake yawan ziyartar ta a ganin ta ƙaunar da yake yi mata ne take sake hauhawa a zuciyar sa da daman take tantamar kamar ƙaunar da ita take yi masa yafi wanda yake yi mata yawa , Sai dai yadda yake yawan taɓa ta tare da bayyana mata cewa shi fa a sarari a matse yake da ita yana da muradin ta , lamarin yana damun ta , domin ita ta san bata cika ƙarfi ba muddin akan ƙaunar Ghaddafi ne , sannan.ta ɓangaren gangar jikin ta ma rarrauna ce . Cikin haka abunda take ƙoƙarin gujewa ya auku , shaiɗan tare da tsantsar son da take yi masa ya sa ta bashi kan ta a wani dare , Daga lokacin kuma sai gurɓacewa ta shigo cikin soyayyar tasu domin tamkar busa ake musu ko umarni , koyaushe suka haɗu sai sun yi ta'asa kafin su rabu , a hakan daga zuciyoyin kowannen su niyyar auren juna bata sauya ba , a ganin su zinar da suke ba kome bace tunda aure zasu yi illa ƙarawa juna so tare da ƙoƙarin kiyaye juna daga zuwa ga waɗansu mutanen daban  ( abunda matasa dayawa suke ta'alaƙa ƙazamtatciyar rayuwar su akai , ba kome bane illa tsagoron son zuciya da rashin shan tsabga da ace ana zane matasan mazinatan da duk aka kama da laifin zina a nahiyar mu kamar yadda addini ya tanadar da abun ya ɗan ragu ) . Daren yau bayan sun gama fasiƙancin su a ɗakin otel ɗin da musamman Ghaddafi yake da ɗakin sa ,    Yake sanar da Maimounatou kan cewa tafiya ta kama shi zouwa Benin da zai iya kaiwa tsawon kwanaki goma kafin dawowar sa da zuwa lokacin kwanaki biyu kachal ya rage tayi jarabawar ta,  ta ƙarshe  .    Ba domin ran ta ya so ba suka yi bankwana washegari da safe da alƙawarin zasu dunga yin waya koyaushe ,  ya kama hanya bayan ya ajiye ta a bayan makarantar su . Sun cigaba da yin waya har kwanaki uku bayan tafiyar sa kafin daga baya kuma ta daina samun wayar sa , shima kuma bai ƙira ta ba , ta damu ainun saboda hakan ɓakon lamari ne a gare ta su shafe tsawon wasu kwanaki ba tare da sun yi magana a waya ba ko da kuwa baya ƙasar . Wasa-wasa sai da suka shafe tsawon kwanaki shida babu waya a tsakanin su zuwa lokacin hankalin maimounatou ya kai ƙurya wajen tashi , jarabawar ta ma sai tayi da gaske take iya rubutawa , Bata da aiki sai gwada ƙiran layukan sa da duk take da su , cike da fatan ko Allah zai sa ta same shi , Bayan ta fito daga jatabawar ta ta yau waje ta samu daga can gefe ta zauna tana cigaba da lalubar layin Ghaddafi , amma kamar koyaushe cikin kwanakin duk layukan sa basa tafiya  , Tsumu tayi a zaune idanun ta cike da ƙwalla , hirar da ta ji wasu matasa na yi daga gefen ta ta ɗan ɗauki hankalin ta , inda ta ji suna labari akan jajirtatcen sojan ƙasa Youssouf ɗa a wajen sarkin Maraɗi wanda cikin watanni da basu cika uku ba , a kwanaki biyar da suka wuce tawagar sa da yake jagoran ta ta tarwatsa gungun ƴan fashi da makamin da suka yi mafaka akan tekun rairayin saharar tenere da yake boda tsakanin Niger da Chad ta yankin Bilma dake ƙarƙashin jahar Agades. An kashe mafi yawa daga cikin ɓarayin manya daga cikin su kuma sun gudu , ciki har da shugaban su da ba'a kai ga sanin cikakken sunan sa ba amma bayanai sun tabbatar da cewa ɗan asalin ƙasar Mali ne . Kalmomin yabo iri-iri suka dunga yiwa Biyamuradin maraɗawa , bayan sun gama tsinewa ƴan fashi da makamin suna kuma fatan Allah yasa a kai ga samun nasarar kashe sauran da suka rage ko Al'umma sa yi kai-kawo a tsakanin ƙasashe cikin kwanciyar hankali , Ita bata wani ji abun burgewa ba , idan ba lalacewa ba me yakai ɗan sarki Yarima a yadda ta ji sun faɗa , yin aikin soja bauta ?wannan ai shine a aiki kare ya aiki wutsiya . Miƙewa tayi tana nufar wajen da ɗakin kwanan ta yake sai dai kafin ta ƙarasa ta ji wayar ta na kiɗan shigowar ƙiran Ghaddafi , cike da ɗoki ta daga wayar tana ajiyar zuciya tamkar wacce tayi gudu . Cikin abunda ke ƙasa da mintoci goma sha biyar tayi shiri cikin doguwar ɓakar rigar ta ta rufa hula baƙa a kan ta tare da rufa ɗankwalin rigar da ta kare rabin fuskar da shi tundaga kan ta , ta nufi babban wajen hutawar da Ghaddafi ya sanar mata yana jiran ta a wajen ta je ta same shi . Yadda ta gan shi duk a firgice da ƙananun raunika a fuska da hannuwan sa da suke sarari ya duƙushe tasirin farin-cikin ganin sa da tayi , sai ta shiga tambayar sa kan ko hatsarin mota yayi ? Ko kuwa ƴan fashi ne suka tare sa akan hanya ,? Bai bata takamai-mai ɗin amsa ba a madadin haka wata sabuwar sallama ya shiga yi mata cikin sanar da ita sabuwar tafiyar da yake da nufin yi a yau zuwa France , da yace yana iya kaiwa watanni biyu zuwa uku , Da wani irin yanayi na tsoro take kallon sa , yaya zai tarki yin tafiya haka mai nisa bayan yasan suna mataki na ƙarshe ne na gaf da cikar burin su me hakan ke nufi ? Duk yadda ta so ta masa rigima yaƙi bata dama , dole ta yadda suka yi sallama ,cikin kwantatciyar muryar sa ya cigaba da rarrashin ta kafin wayar sa take danƙe a hannun sa tayi ƙarar alamun shigowar saƙo , yana karanta saƙon ya miƙe a ɗimauce yana raba ganin sa a da'irar wajen hankalin sa baki ɗaya ba'a kwance yake ba , da ido ta bi shi ƙwalla na taruwa mata , yadda ya juya bai ko saurare ta ba , ya taɓa mata rai babu shakka akwai abunda yake faruwa da shi da bata kai ga sani ba , taku biyu yayi ta ƙira sunan sa , a hankali ya juyo yana ɗora ganin sa akan ta tsayayyun idanun sa na bayyana wani irin yanayi na tsoro . " Ghaddafi , kada ka manta da ni zan jira ka koume tsawon lokaci , ta furta hakan tare silalowar hawaye daga kwarmin idanun ta , Daga inda take ta hango yadda laɓɓan sa suka motsa ko da kunnuwan ta basu iya jiyo mata amon sautin kalmomin sa ba ta fahimci cewa cewa yayi ,     " Maimounatou ina son ki . Ƙarar harbin bindiga da ya gifta ta kunnen ta shi yasa ta kusa hantsilawa daga kan kujerar da take zaune ,  kafin ta farga harbe-harbe sun yawaita a sararin wajen da nan take mutane suka kaure da guje-guje , akan idanun ta Ghaddafi ya ɗaga kafafunsa ya taka da gudun gaske yana barin wajen kamar fitar kibiya . Ta miƙe tsaye amma ruɗani ya sa ta koma da ƙarfi ta sake zama tana toshe kunnuwan ta biyu , ta gaban idanun ta takun ƙafafun sa da suke sanye da manyan takalman sa na soji ya wuce da gudun gaske ya dafa baya akan hanyar da Ghaddafi ya bi . Ba zata iya sanin iyakar adadin mintocin da tayi durƙushe a gurin ba, zuwa lokacin da harbin bindugogin ya tsagaita , lokacin ta samu damar miƙewa daga durƙuson da tayi a ƙasan teburin gaban kujerun wajen . Ba tare da ta tantance yanayin da take ciki ba ta fara taku da sauri da niyyar ficewa a wajen , can gefen zuciyar ta na son sanin halin da Ghaddafi ke ciki , sai dai bata saurara ba domin tana buƙatar nutsuwa mai tarin yawa a dai-dai lokacin . Kamar ance ta ɗago kan ta lokacin da ta ɗaga ƙafa tana barin wajen , idanun ta suka sauƙa kan dogon sojan da yake sanye da kakin sa da jini ya ɓata gaban rigar , har yana ɗiga ta wajen hannun sa ,  yana tafe da takun sa na jarumta a hankali ta sauƙe ganin ta ƙasa inda ya riƙo ƙafar mutumin da ya harbe yana jaan sa tamkar kayan wanki , idanun ta suka sauƙa kan fuskar Ghaddafi da jinin da ya ɓata fuskar sa zuwa ƙirjin sa bai hana ta gane shi ba , Duk wasu jijiyoyin jikin ta ne suka tsayawa yin aiki , jinin ta ya daskare , kamar yadda kunnuwanta suka toshe , numfashi kuma ya fara kokawar kufce mata , ƙafafun ta taji suna mata girgiɗi.     " Ya kashe min Ghaddafi , Ya kashe min Ghaddafi . Sune kalmomin da suka ƙwanƙwashi ran ta suka farkar da ita daga suman zaune da tayi , wani irin ihu ta sa mai sauti da ya jawo hankulan tsirarun mutanen da suka rage a wajen da zuwa lokacin daman ma'aikatan wajen ma korar jama'a suke . Babu wanda ya saurari kukan da take yi da ake zaton na firgici ne aka tisa ƙeyar ta zuwa wajen park ɗin . Mutuwar Ghaddafi bata zowa Maimounatou da sauƙi ba domin tamkar hauka tayi , surutai kawai take yi tana sambatun da ba'a wani fahimtar me take cewa , bata rubuta jarabawar ta ta ƙarshe ba hukumar makarantar ta turawa da Maimartaba mummunan saƙon rashin lafiyar ƴar sa , Nan take aka tado da mutane ciki har da manyan yayun ta suka zo Niamey suka  ɗauke ta zuwa gida Agades . Kowa ya ga yadda take yi a lokacin cewa ake gamo tayi , aljannu ne suka taɓa ta, dan haka aka shiga magungunan iska ba ji ba gani , Ganin ana ta banka mata hayaƙi babu gaira ba dalili , ya sa ta rusuna ta bar surutai da ƙiran sunan Ghaddafi , sai ta koma ba un ba un'un , bata iya ci bata iya shan ruwan kirki wanka ma bata yi , Ba'a tsahirta da magunguna ba , aka cigaba da kawo magani iri-iri , na wanka da na sha da na turare , kai har da na shafawa da shaƙawa , Mafi yawa zubda su take yi , ta kuma kasa sanar da kowa dalilin tashin hankalin ta , to cikin iyayen ta biyu wanene ya san Ghaddafi ?? Ya san Alaƙar su ? Babu . Tsawon wata guda ta fara dangana sai kuma rashin lafiya Mai tsanani ya taso ta a gaba , ciwon ciki mai tsanani duk ɗan abunda ta samu ta ci sai tayi aman sa , ga zazzaɓi mai zafi tare da ciwon kai , Kasancewar ta wayayyiyar ƴar jami'a ita da kan ta ta fara bincikar kanta game da sauyin yanayin da take ji a jikinta  , a sirance ta aiki Gnala ta sayo mata abun awun tabbatar da samuwar ciki . Da zaton motsuwar kwakwalwar ta Gnala ta karɓi kuɗin ta sayo mata , Kamar yadda tayi zato gwajin farko ya nuna mata samuwar ciki a jikin ta , Ranar damuwa ta dawo mata sabuwa dal , tayi kuka irin wanda tun mutuwar Ghaddafi bata samu damar yin irin sa ba sai ranar , " ina zata da cikin jikinta tana ɗiyar Martaba ɗiyar Asali ɗiyar sarki ?? Ya zama dole ta rabu da cikin , ina ma da ace aure suka yi ita da Ghaddafi ta samu cikin nan ? Da zata fi kowa murna da samuwar sa , Ita da kanta ta saci hanya ta fita , wani babban ɗakin sayar da magani ta je , bayan ta wadata mai sayar da maganin da maƙudan kuɗaɗe ya ɗau maganin zubar da ciki mai ƙarfi  ya bata , Tun da ta saya maganin sau uku tana yunƙurin shan maganin tana kasawa , cikin satin gaba ɗaya ta sake lalacewa ta rame tamkar wacce take tsananin ciwo , A karo na huɗu ta runtse ido ta haɗiye maganin , ta yi kamar yadda pharmacist din ya faɗa mata , Cikin ƙasa da mintoci arba'in kachal jini ya fara sauƙa mata kafin ciwon ciki mai tsanani ya biyo baya , jini kuma ya ɓalle mata , Kasancewar ta kulle ƙofar falon ta bayan ta kori bayun da suke kula da ita sai Gnala kaɗai ya sa babu wanda ya san irin wahalar da ta sha da irin zubar jinin da tayi daga ita sai Gnala , Da kyar jinin ya dai-daita ciwon cikin kuma ya lafa ta samu bacci , Sai zuwa la'asar ta farka ta ji ƙarfin jikinta duk wasu kasala da rashin ƙarfi irin na masu ƙaramin ciki ta rabu da jin su ,  dan haka tayi wanka ta shirya tana jin raguwar damuwar da take ciki da kaso goma cikin ɗari , Kai tsaye sashin Mahaifiyar ta ta yiwa tsinke , inda ta tarar da ita a babban falon ta tana kishingiɗe bayu na mata hidima , ganin ta ya sa ta miƙe zaune cike da jin daɗi ta rungume ta tana murnar ganin alamun samun lafiyar ta , Duk da cewa ta hango wasu yanayi da bata gane da su ba a tare da ita amma ta danganta kome da larura irin ta jinnu da babu abunda basa sawa . Suna zaune aka hasko fuskar Colonel Youssouf Abdoul-azizou baskore a babban tv da yake kafe a gaban su , ana bayani akan ƙarin girman da ya samu sakamakon samun nasarar kawo ƙarshen gungun 'yan fashi da makamin nan da ake yiwa take da escouade de lions , inda bayan rundunar su ta tarwatsu su daga terene , ya samu nasarar kashe manyan huɗu daga cikin su , ciki har da shugaban su Ghaddafi Yacouba Dango .   Raba hoton aka yi biyu , gefe hoton gawar Ghaddafi ne , gefe kuma hoton Youssoufa ne yana dariya lokacin da ake masa ƙarin girma . ****    Gimbiya Maimounatou ta sanya hannuwanta biyu ta share hawayen ta , kafin tayi ƴar dariya da take nuni da tasowar miƙin ƙasan ranta ta cigaba da cewa " Tun daga wannan ranar na kuɗurci aniyar ɗaukar fansa akan sojan da ya kashe Ghaddafi da hannun sa , nima so nake na kashe shi, so nake na ɗanɗana masa baƙin-ciki irin wanda ya samar a gareni .      " Ban damu da laifin da ake tuhumar Ghaddafi da shi da yasa aka kashe shi ba , a ganina Ghaddafi bai cancanci mutuwa a yanzu ba kome kuwa girman laifin sa , akwai sasauci hukuncin kisa yayi tsanani ga Ghaddafi , mafi girman sashi na raina ma ban yadda da laifin da aka danganta Ghaddafi da yi ba , saboda ni ban taɓa ganin sa yayi kisa a gabana ko satar kayan wani ba .   " daga lokacin na shiga bin hanyoyin da duk nasan zasu taimaka min wajen cimma nasara kan ƙudiri na , a ƙarshe kuma nayi nasarar sanyawa Youssouf so na da har ta kai ga ya amre ni sanin da nayi wannan ce hanya mafi sauƙi da zata kaini ga kashe shi , " ga jin daɗina lokacin da nake bibiyar rayuwar sa ina kafa masa tarko bayan auren mu , sai na fahimci ba ni kaɗai bace ba ke farautar rayuwar sa , ciki har da kai da Mahaifiyar ka Mammadou , babu ɓata lokaci muka haɗa hannu wajen ganin ƙarshen maƙiyin mu , kuma ga shi a ƙarshen ƙarshe mun yi nasara ,   Wata ƴar dariya ta sake yi tana tsare ɗan sanda da ido , tace " wai ya ƙarasa mutuwa ne ko kuwa har yanzu yana shan wuya ?     Wani ƙaƙƙarfan marin da aka ɗauke ta da shi da ya sanya ta yin tangal-tangal tare da giftawar walƙiya a idanun ta ya sanya ta rufe bakin ta ruf , Da wani irin yanayi a muryar Tafeeda yace ,   " Babu shakka kin kasance mayaudariya , azzaluma ban yarda ke kina da ɗigon imani ba a ran ki , kamar yadda kika ce hukunci wanda yayi kisa ko ta yaya ne a kashe shi a irin naki ƙwaƙwalwar mai cike da duhun jahilci , da ke da duk wasu masu hannu cikin wannan mummunan aikin da kuka yiwa Youssouf muddin ya kai ga rasa ransa kamar yadda kuka so , wallahi baki ɗayan ku sai na kashe ku da bakin bindiga ta koda kuwa hukunci ya so muku sassauci , ni sai na kashe ku , sai na ....   Muryar sa ce ta sarƙe jikinsa har tsuma yake idanun sa sun koma ciki tsabar tashin hankali , ya juya da sassarfa ya fita zuciyar sa cike da ruɗani ashe masoyin ka da ka yadda da shi kan iya zama mai farautar ranka ? Da ya tuno irin tsananin son da Youssoufa ke yiwa Maimounatou sai hawaye ya sauƙa a idanun sa , wacce irin zuciya ce haka a ƙirjin Mammadou da Hajiya Mama da zai sa a haɗa baki da su wajen kashe mutum irin Youssoufa shin me ya taɓa yi musu da zafi da ya cancanci ƙiyaya irin haka ? Babu shakka mutum ya tsoraci maƙiyin sa da yake ƙin sa babu wani dalili bayan ta hassada , irin wannan ƙiyayyar mai zafi ce , tsawon zamani baya tasiri wajen goge ta . Yana kai ga ficewa daga harabar ofishin motar su Maimartaba da kansa ta sawo kai dan haka yayi baya da tasa motar tare da sake kashe ta ya fito , Sama-sama suka gaisa da Maimartaba a tare da shi da mahaifin shi kansa Tafeeda , sai kuma Hajiya Mama su uku ne kawai tare da direba , Hajiya Mama tayi firi-firi da tashin hankali ta bi bayan su Maimartaba , Tafeeda ya dafa musu baya yana jin kamar ya shaƙe Hajiya Mama , A ciki kai tsaye suka nemi da a haɗa su da Maimounatou da Mammadou , Bayan shigar su inda suke da har lokacin kowannen su bai rusuna ba , Mammadou yana ganin iyayen sa ya fashe da kuka yana ƙaryata duk wasu kalmomin da Maimounatou ta yi , akan yana da hannu wajen kisan Youssouf ,   " Ranka shi daɗe wallahi ƙarya take min ban san kome ba , bani da hannu wajen mutuwar ɗan ouwana wallahi Abba ƙarya take min , Cike da nutsuwa Maimartaba yake kallon sa , kafin yace    " Mammadou , Youssoufa bai kai ga mutuwa ba , har kawo yanzou yana asibiti , zuwa nan nayi saboda na fidda kai ne daga nan muddin ta tabbata baka da hannu cikin lamarin nan , muddin kuwa aka kama ka da laifi ni bani da ikon hana mahukunta aikin su , zaka cigaba da zama a nan har zuwa yadda hali zata kasance ga Youssoufa tsakanin rayuwa da mutuwa , daga nan sai mahukunta suyi hukuncin su yadda ya dace .    Wani irin runtse ido Maimounatou tayi , tana son cewa wani abu sai dai cikar kamala da ƙima irin ta Maimartaba ya wuce ta yi wargi a gaban sa , Hajiya mama wacce ganin hawaye tare da tashin hankalin da ɗan ta yake ciki tare da kalaman da Maimartaba ya furta suka haɗu wajen ƙara mata tashin hankali kan wanda take ciki , ta zaburo tana cewa ,   "  Ni nasani Mammadou ba zaka yi yunƙurin kashe ɗan ouwan ka ba , na san irin tarbiyyar da na yi maka , ni shaida ce akan irin ƙaunar da kake yiwa ɗan ouwan ka sai dai idan wannan makirar ce take ƙoƙarin samun abokin da zata raba laifin ta da shi , shine zata maka sharri , tsinannan ibilishiya ta Allah ba taki ba Youssouf zai tashi bai mutu ba ,     Ta ƙarasa zancen tana fashewa da kukan wanke kai ,   Kukan nata bai tsawaita ba ta tsinkayi muryar Maimounatou tana cewa ,   " Hajiya kenan, ai ibilisan muna da yawa , amma ke ce shugabar mu , idan kin ce sharri na yiwa ɗan ki akan gubar da na zubawa Youssouf dan an samu tangarɗar cikar aiki , asirin da kika yiwa Youssouf na shan giya da neman mata domin ya tozarta ya rasa damar samun sarauta shima sharri ne kenan ? Duk da cewa kowa ya shaida saboda har ɗiyar banza Youssoufa ya ajiye aikin ki kuma ya kai ga matakin nasara kamar yadda duk kika tsara Youssoufa ya rasa martabar sa a idanun Al'umma , Kukan kura Hajiya Mama tayi ta shiga dukan Maimounatou , tana cewa ,    " sharrin ki kaina zai dawo ? wallahi ranka ya dade ƙarya ɗiyar nan take min so take ta ga bayana , so take na tozarta shi yasa take faɗe-faɗen surruka masu nawi . Maimartaba bai ce ƙala ba ya juya ya fita , yana fita , Maimounatou ta tunkuɗe Hajiya Mama da ƙarfi , cikin tsawa tace ,     " Saurara ɗiyar talakawa , mai gajaren asali ni nan da kike gani na ɗiyar sarki ce , sarkin da ya yafi duk wani sarki ƙarfin mulki a ƙasar nan ,  dan haka ahir ɗin ki da ki sake taɓa lafiyar fatar jikina , kiyi ta kan ki da ramin da yake gaban ku ke da ɗan ki,  idan ku ka faɗa babu mai iya cire ku , ni kuwa kin ganni kome girman ramin da na faɗa daga Mahaifina ya ziro hannu zai tsamo ni . Kamar wacce aka yiwa umarni Hajiya Mama tayi hanzarin barin ɗakin zuwa inda su Maimartaba ke tsaye suna sauraron muryar duk labarin da Maimounatou ta bayar ,da ƴan sanda suka naɗa a waya . Bai jira karshen labarin ba Maimartaba yace su tafi kawai , jami'an tsaro su cigaba da yin aikin su duk ta yadda ya dace da ƙa'idar aiki , shi hankalin sa baki ɗaya yana ga Youssoufa da yake asibiti cikin mummunan yanayin mutu-kwakwai rai-kwakwai  da a halin yanzu an gama shirin kome na fita da shi ƙasar India , lokacin tashin jirgin su kawai ake jira nan da awanni uku . A gidan baya na motar da Hajiya Mama da Maimartaba suke zaune , banda raba ido cike da rashin gaskiya babu abunda take yi ƙwarai Kalaman Maimounatou a gaban Maimartaba suka shammace tare da ƙara mata tashin hankali , ganin kome na shirin kwaɓe mata cikin ƙanƙanin lokaci . Muskuɗawa tayi tana kallon Maimartaba tayi ƙanƙan da kai ta fara cewa ,     " wannan ɗiya lamarin ta abun tsoro ne, dukkananin kalamanta cike suke da ƙarairayin.... Da hannu ya dakatar da ita ba tare da ya dubi sashin da take ba yace "  Su kalaman mutum suna iya zamar masa tarko su fallasa ko wanene shi , ita hanyar mugaye kuwa duhu ne baƙi ƙirin, kamar duhun dare , da har sukan faɗi a cikin turbar su amma ba su san abin da ya sa suka yi tuntuɓe ba , sukan manta da cewa ita mugunta rami ce mai zurfi da a ƙarshe da mai tonon ta take ruftawa ciki , ki adana kalaman ki akwai wajen yin su ba nan gabana ba . Muƙut ta haɗiye busasshen yawun tashin hankali , ta san irin wannan zaurancen na masu hikima da mafiyawancin lokuta Maimartaba ya fi amfani da su cikin kalmomin sa . Hasashen manufar kalamansa ya sa gumi karyo mata yana tsiyaya ta cikin jikin ta , " Babu shakka kwaɓarta tayi ruwa tsululu . **** Ƙarfe biyu na ranar jirgin da zai tafi ƙasar India ya ɗaga da Youssoufa yana a halin rashin sanin ina yake ?  A tare da shi da Maimartaba da kansa , da Hajiya Umma da kuma Tafeeda . Tamkar wutar daji haka labarin gubar da Matar Biyamuradi Youssoufa da ɗan ouwan sa Mammadou suka ciyar da shi ya shiga ratsa kowanne lungu da saƙon ƙasar Niger baki ɗaya , Cikin kwanakin duk wasu kafar yaɗa labarai zancen ake ana sake maimaita sa , har wani sashi na daga muryar Maimounato cikin labarin da ta bayar kan dalilinta ake sakewa , A halin haka labari ya shiga sauya salo da launi iri-iri dake ƙara munana sa , wasu ma cewa suke ai fasiƙanci Maimounatou da Mammadou suke yi , da kuma sanin ita uwar Mammadou ita ce ma ta bada gubar da aka ciyar da Youssoufa ita . Tozarta da ɓacin suna irin wanda Hajiya Mama bata taɓa zaton afkuwar sa a gare ta ba , ita ce ta faɗa mata lokaci ɗaya , Tuntuni labarin irin auka-aukar da Maimounatou tayi ya iske kunnen iyayen ta , da hakan ya sa take jinin Maimartaba sarkin Agades ya hau , aka ciccɓe shi ranga-ranga zuwa asibiti . Nan take wasu daga cikin dangi suka fara Allah wadarai da ita .       Assalamu Alaikum masu karatu da fatan kuna lafiya ? Ina sane da haƙurin bibiyata da kuke yi , ina kuma godiya bisa yawan ƙaunar ku ga rubutuna nagode irin sosai ɗin nan , nima ina ƙaunar ku a duk inda kuke ina muku fatan Alkhairi . Nagode [12/26/2019, 9:58 PM] +234 706 503 6187: MAFARI ( Hargitsin Rayuwa) Umm'muaz 47 Falmata tun tana zuwa ɗakin Hajja tayi ta zama ba tare da ta iya faɗin abunda ke kaita ɗakin ba , Har dai a kwanaki shida bayan zuwan su ta daure bayan sun gaisa da Hajja wacce take kishingiɗe akan ƴar katifar ɗakin ta , ba tare da ta yadda sun haɗa ido da Hajja ba tace , " Hajja daman zuwa nayi nace miki , un'un wai inji Baa , sai kuma tayi shiru , Hajja wacce ta tashi zaune , tace , "Uwarɗakina faɗi mana , me kike son faɗa min ? "Daman nace Hajja idan kun yi waya da shi ki ce masa akwai saƙon da nake son faɗa mi shi inji Baa , Kallon tsanaki Hajja take yi mata kafin ta ce , " Shi wa fa ?   Ɗago kanta tayi ta saci kallon Hajja , tana sake gintse fuska tace , " shi Baban Mama ko ? Salati Hajja ta sa tana tafa hannuwa , kafin tayi ƙanƙan da ido tace ,    " Ke Fatima ki fita idona na rufe ,nace ki fita idona ,  idan ba kin mayar da kanki wata bi ta can ba , har kya bani saƙo wajen Mijin ki ? Cewa nake ke kika fi kusanci da shi fiye da kowa a ƙasar nan ? To bari na faɗa miki daman ina cike da ke akan irin sakarcin da kika yi na gudowa daga ɗakin auren ki , akan wannan mummunar zuciyar taki mai ƙullaci da bauɗaɗɗan halin ki na miskilanci idan baki gyara kin nutsu kin san ina ke miki ciwo ba ke ce da Nadama marar amfani wataran , ni nagaji da nuna miki gabas kina daɗa bauɗewa, Zunburo baki Falmata tayi , ƙasa-ƙasa tace " to ai ba komawa zan yi ba , Ashe maganarta ta shiga kunne Hajja , sai ji tayi tace ,   " Auho aikin kawai kike domin shima kuwa wannan karon kin kai shi bango da iyashegen ki , dan tunda muka taho yau kwana shida muna yini na bakwai bai biyo sawun mu ba ko da da ƙiran waya , ni kuma na ƙira layin nasa da nake da shi bai tafiya , ai kin ga sai ki zuba ruwa a ƙasa ki sha , idan zaman gidan daɗi ne ki zauna ga waje kiyi ta zama har mahadi ya bayyana . Daga haka ta jaa bakin ta ta tsuke tana kawar da kai . Rai a ɓace Falmata ta miƙe ba ko sai anjima ta fice a ɗakin , Hajja ta bi bayan ta da kallo , cikin ran ta cike da tausayin ƙuruciyar dake ɗiban ta tana shirin sanyata yiwa kanta sakiyar da ba ruwa , ita a karan kanta ba ƙaramin damuwa tayi ba da rashin ji daga wajen Youssouf kamar yadda yace kafin rabuwar su zai ƙira domin jin labarin halin da suke ciki , rashin ƙiran nasa ya ɗaure mata kai , tsoron ta ɗaya kada ace ya sau auren Falmata , ko kaɗan bata fatan hakan , tayi ƙiran wayar sa aƙalla sau goma bayan tahowar su amma bata shiga fatan ta Allah yasa lafiya . Haka kawai ta ji damuwa tana mamayar ta kan cewa da Hajja tayi tunda suka taho wai bai ƙira ba , ita a nata zaton su na gaisawa da Hajja ta waya , kawai bai neme ta bane sanin da yayi tana fushi sosai da shi dan haka ko an kawo mata wayar ma ba karɓa zata yi ba kamar yadda ita ma ta kuɗurce a ran ta , To ashe ma ita take zaton haka shi yana can ko tunawa da sha'anin da ya shafe ta baya yi , ya riga ya yada da ita da abunda ke tare da ita , duk sai jikin ta ya sake yin sanyi ƴar hirar da suke yi ma ita da Yakaka da Rahima ƙarama kafin tashin ta zuwa ɗakin Hajja,  sai ta gagara cigaba da sa baki tayi lamo a kwance tana jin yadda abunda ke cikinta yake dunƙulewa waje guda , Yakaka ita ta lura da shirun da tayi dan haka ta kai hannu ta jaa yatsar ƙafar falmata tare da cewa ,   " Maman baby yaya ne ? Akwai damuwa ne ?   Janye ƙafar ta tayi ba walwala a muryar ta tace ,    " Maman mama kin san dai na ce ku daina ƙirana da sunan nan bana so , Rahima ta kwashe da dariya "  to Yakaka mu daina cewa Maman Baby , mu koma ƙiran ta da Matar soja yafi daɗi ko Hajja Falta ? Kuka ta fashe da shi da a farko suka yi zaton na wasa ne , sai da suka ji har tana jaan hanci tukun suka tsahirta daga dariyar da suke duk kuma sai hankalin su ya tashi jikin Yakaka har rawa yake ta tallafo Falmatan zuwa jikin ta suna rige-rigen tambayar ta " me ya same ta take kuka ??    Ba tare da ta daina kukan ba tace ," Nace muku bana so  , bana so bana so , kun ƙi dainawa .   Da sauri Rahima tace , " Yi hakuri ba zamu sake ba dan Allah ki daina kuka daga wasa ? Haba Fatima-zahra Maman Baby ,    Da sauri Yakaka ta ɗago tana hararar Rahima ,    Dariyar da Rahima take bata tuƙe ba ta dafe baki tare da cewa    " Au So nake nace Mamar Mama ta biyu , yi haƙuri ba zamu sake ba kin ji ƴar ƙanwata ? Batare da ta amsa ba ta zame daga riƙon da Yakaka tayi mata ta koma ta kwanta a inda ta tashi , wani irin yanayi marar daɗi na sake mamayar ta baki ɗaya bata jin daɗin kome , abu kaɗan sai ya ɗaga mata hankali ya ƙara mata damuwa .   Fuskar Yakaka cike da damuwa take kallon ta , damuwar da ta hango tare da ita ya ɓata mata walwalar da take ciki mai daɗi , cikin ran ta ta haƙiƙance akwai abunda ke damun Falmata haka kawai ba zata yi kuka ba daga ɗan wannan wasan , ji tayi ta damu da son sanin damuwar ƙanwar ta  . Tun daga ranar sai duk walwalar ta ta ragu damuwa ta bayyana a cikin suffa da mu'amalar ta , kome take yi babu nishaɗi duk kuwa da cewar basu taɓa tsintar kan su a cikin gata da riritawa irin na wannan lokacin ba , daga kan Mamar su har zuwa Amnee da Baa , Rahima da kusan kowa na gidan nan-nan ake da su , Sai dai damuwar ta mai zurfi ce , kullum cikin kasa kunne take ta ji ko Hajja zata ƙira ta tace ga Youssouf ya ƙira su yi magana ko kuwa ma tace ya ƙirata ita sun gaisa amma ko alama ta yin ƙiran nasa bata ji ba , ita kuma tsoron surutun Hajja ya sa ta kasa tambayar ta . *** Yau tana zaune a tsakanin mamar su da Amnee suna ƴar hira , su ukun ne kawai a wajen , Rahima da Yakaka sun tafi amso sabbin ɗinkunan su da Baa ya bayar da kuɗi aka kawo musu atamfofi da lesika aka kai ɗinki domin su yi amfani da su wajen bikin auren Rahima da yanzu bai fi kwanaki goma sha biyu ba suka rage . Amnee ta ɗan dube ta tana murmushi tace ,    " Fatima zahra , cikin nan naki wata nawa yake ciki ne ? Anya bai kamata ki fara zuwa awo ba ?   Da sauri ta ɗago kai ta dubi Amnee sai kuma ta sunkui da kai batare da tace kome ba , Khaalty Rahima ta ɗan dube ta , tace Fatima ba dake ake ba ?   A hankali tace , " Nima ban sani ba Amnee , Jimm Amnee tayi kafin ta ce , " to ai ya kamata ki fara zuwa awo banda ma dai shirme irin naki Fatima cikin fari da ake ɗokin sa da yi masa ƙirgen ƙwaƙwaf amma ke kyace baki san watannin sa ba ? Hajja wacce take ƙarasowa falon daga waje inda ta gyara shanyar alkamar da ta wanke ta yin kunun Baa , sarai ta ji wasu daga kalaman Amnee , tace    " Wallahi uwar masu gida ke ma dai kya faɗa , wannan uwarɗakin tawa da kike gani kome nata daban ne bata ajiye kome ba sai wauta , cikin nata yana gaf da cika watanni huɗu a yadda lissafi na ya nuna min , sai dai kuma kin san cikin fari ɓuya ce da shi amma lokacin da suka dawo dai daga can turai cikin bai wuce watanni biyu ba da ƴan ɗoriya , daga can ta yo cikin ,  yanzu kuma kin ga dawowar tasu kusan kwanaki talatin . Dariya ce ta so kama Khaalty Rahima jin wannan ƙokari na Hajja na ƙididdige kwanakin cikin Falmata da ko ita kakar ɗan ko ƴar ba ta iya haka ba , Ran ta cike da jin daɗin tsantsar ƙaunar da ta lura Hajja na yiwa ƴa ƴan ta tace ,   " Hajja baki da dama ke da Uwarɗakin ki ba mai shiga tsakanin ku , wannan zuwa awon ma ai ke zaki dunga raka ta  .   Ƴar dariya Hajja tayi kafin ta harari Falmata tace ,     "  can dai su ƙarata ita da Babba Uwar Mama ita zata raka ta bana iya miskilancin fatima ba . Dariya Amnee tayi kafin tace,   " zan yi maganar da Baa Alaji idan ya so sai ya nema mata iznin mijin nata , kan fara zuwa asibiti saboda kuwa zuwa awo abune mai matuƙar muhimmanci ga mata masu ciki , yadda duk muka yi sai ki shirya a fara kai ki kin ji ko ƴata ? A hankali ta gyaɗa kai kurum , tausayin abunda ke cikin ta kan yadda Mahaifin sa yayi banza da su ya fara kamata . Daga haka Amnee da Mama suka cigaba da yin hirar su , a hankali ta miƙe ta nufi ɗakin su , domin kuka da take jin yana taso mata , Tana shiga ɗakin ta sanya tafukan ta duk biyu ta rufe fuskar ta tana fashewa da kuka marar sauti . Tana tsakiya da yin kukan ta tsinkayo Sallamar Doctor Hamza , shuru tayi tana saurarawa jin tashin muryar gaisawar da suke shi da iyayen su , Jin sun gama gaisawa sai ta miƙe tan share hawayen ta , Doctor Hamza yana sawun gaba na mutanen da ba zata manta alherun su ba a rayuwar ta ,dan haka ya zama dole duk inda ta ji shi ta je ta gaishe shi ko da kuwa babu ƴan uwantaka a tsakanin su bare yanzu da suke ƴan uwan juna makusanta , A hankali ta fito , ta tako zuwa tsakiyar falon ta zauna tana gaishe shi , Da murmushi yake amsawa yana jin daɗin ganin ta samu lafiya , yace    " Fatima ƙanwata ke ce haka kika girma ? Alhamdulillah lafiya ta samu . Ƴar dariya tayi , kafin tace " Ni ce Yaa dakta ,   Dariya shi ma yayi yace " lalle girman 'ya mace ba wuya , Al'amarin Ubangiji kuma ya zarta yadda duk muke zato , Khaalty lokacin da na kawo yaran nan gidan nan ko kusa bani da masaniyar muna da wata alaƙa tsakanina da su , kawai nayi niyyar taimakon su ne domin Allah , ashe kin ga ma abun farin-ciki ƙannena ne su , lokacin da Amnee take sanar da ni ba ƙaramin mamaki nayi ba da farko ma ni na shiga ruɗani ne su waye Amina da Fatima ? Sai da ta min bayani sosai , Ya nisa kafin ya cigaba da cewa , " Khaalty nayi murna da Allah ya haɗa ki da ƴaƴan ki , Allah ya kuma kare ku baki ɗaya , ya sa bakin wahalar ku kenan .   " Amin Amin ɗana , tace da sigar zolaya ,   Shima dariyar yayi da sauti sanin cewa ta ƙira shi da ɗanta ne dan tasan bai son haka tun yana ƙaramin sa a cewar sa tayi ƙanƙanta ta ƙira kanta Mamar sa ina ma laifin tace ita yayar sa ce  ?   Khaalty Rahima ta cigaba da cewa , " kawai sai muka gan ka babu sanarwar zuwa ? Ko wani aikin ka zo yi ?   Jingina kansa yayi da kafaɗun kujerar da yake kai , yace   " Baa ne ya ƙirani tun shekaran jiya , yace lalle na zo cikin kwanaki biyun nan , to nima daman kuma ina shirin zuwa saboda shirye-shiryen bikin nan ban sani ba ko akwai abunda za'a iya buƙata mai muhimmanci ayi a gama akan lokaci tunda ga ku , kar ya zama irin na bikin su zainab kome a hagunce , aiki ne ya tsare ni ban iso da wuri ba .   " Na fara shiga wajen Baa ɗin amma na tarar da shi da mutanen nasa kin san sai kuma ya sallame su da abunda suka saba , kai mutanen mu sai a hankali , wai kawai sai ku mayar da wani mutum ɗaya wajen zuwa ku faɗi buƙatun ku da damuwar ku kamar wani shi ɗin injin buga kuɗi gare shi ? To wai wanene bashi da buƙatu da damuwowi ? Sallamar Rahima da ta shigo da ɗan gudun ta , ya sa shi mayar da ganin sa kan ƙofar , dai-dai da shigowar Yakaka , wacce tunda ta ji Rahima na murna tana cewa ga motar Company ya zo , ta ji jikinta yayi sanyi duk taku ɗaya na kafafun ta da jin ƙarin hauhawar bugun zuciyar ta , Idanun ta ta sauƙe kansa da shigowarta falon , karaf suka haɗa ido , Kowanne su yayi saurin janye ido Doctor Hamza ya haɗa da kawar da kai ita kuma ta sunkui da kan ta , cikin raggon taku ta ƙaraso ta bayan kujerar da Amnee take kai , tayi durƙuso da kyar ta haɗo kalmomin ,    " Ina wuni ,   Kamar bai ji ta ba haka ya cigaba da zolayar Rahima da yake cewa " ke little idan ana shirye-shiryen aure ramewa ake yi ke kuwa ga ki sai sake kumbura kike , me takwarar ki take baki haka hala ɗure take miki ??    Dariya Khaalty Rahima da Rahima ƙarama suka sa a tare , kafin Rahima ta zagaya ta kujerar da Amnee take ta saƙalo hannuwanta a wuyan ta , tana haɗa fuskokin su tace ,    " Khaalty kar ki faɗa masa , abun sirri ne ko ?   Amnee wacce ta lura da yadda yayi watsi da Yakaka , kuma bata ji daɗin hakan ba sai ta ce ,    " Takwarata tana gaishe ka fa ? Wani wur-wur yayi da ido , sai kuma yace " Ok Lafiya , ba tare da ya dube ta ba illa haɗe girar sa da yayi , ya zaro wayar sa daga Aljihunsa , kaf fara'ar fuskar sa ta ɗauke . A hankali Yakaka ta miƙe tana murmushin yaƙen akan wasan da Mamar su da Rahima suke yi , sum-sum ta wuce ɗakin su . Ƙiran wayar Amnee da aka yi yasa suka ɗan tsahirta daga hayaniya , bayan ta ɗaga wayar sai ta saurara ,   " to Baa Alaji tace.  Duban Khaalty Rahima tayi , tace   " Ukhtee , da ke da Ɗan ki ku zo muje Baa alaji yana ƙiran mu . *** Bayan sun sake gaisawa a tsakanin su ,a ƙagauce Amnee da take zaune daga gefen sa tace   " Baa Alaji lafiya dai ko ? Wannan ƙiran Allah ya sa Alheri ne.  Prof ya dube ta da ɗan murmushi , yace " inshaAllah Alheri ne Aminatu , ganin ya mayar kan Hamza da Khaalty Rahima da suke zaune a ƙasa kafin ya fara cewa . " Dalilin da yasa na ƙira ku ba kome bane sai kan wata magana ko kuwa nace shawarar da na yanke tun watanni baya , amma ban sake haƙaƙewa akan abunda nake niyyar yi ba na haɗa Aure tsakanin Ƴaƴa na biyu kai Hamza da kuma ƙanwar ka Amina ba , sai da tabbatuwar yaran nan ƴan uwan ka ne ba wasu bare ba da ba'a san asalin su ba , hakan ya sa na sake ganin dacewar lamarin fiye da farko , " Duk da cewa batun ƙarin auren da nace kayi ba sabon abu bane a wajen ka , tun kwanaki na sanar da kai ka kuma yi na'am kawai wacce nake burin ka aura ɗin ne baka kai ga sani ba , sai a yanzu nake sanar da kai Aminatu ƴar Rahima ƙanwar Mahaifiyar ka ita ce matar da nake son ka aura a matsayin matar ka ta biyu , da fatan ba zaka yi gardama ba ?? Daga Khaalty Rahima har Doctor Hamza baki ɗaya idanu suka zuba suna kallon sa , a hargitse sosai ƙwaƙwaƙwar Doctor Hamza take , meke nan yake ji ? Yaya Baa zai masa haka ? A hankali ya sauƙe ganin sa daga kan prof ya sunkuyar da kansa ƙasa , ta wutsiyar ido yake hango yadda Khaalty Rahima ta dawo da ganin ta kan sa , zuciyar sa na shaida masa cewa amsar sa kowa a wajen yake jira , kan ya amince ko kuwa a ah  ? abunda ya bi duk wasu gaɓɓai na jikinsa ya kassara bai wuce kaifin idanun Khaalty Rahima ba , matar da tunda ya buɗi ido ya gansu tare da Mahaifiyar sa a matsayin shaƙiƙan juna , ƙaunar ta a gare shi kuma mai tarin yawa ce , jin daɗin wasannin ƙuruciyar sa duk ya yi tare da ita , shi kuwa ta yaya zai iya cewa yaƙi ƴar da ta haifa daga cikin ta a tsatson idanun ta ?  wallahi ba zai iya ba , Baa ai bai kyauta masa ba da ya titsiye shi da wannan batun a gaban idanun Khaalty Rahima , Satar kallon Amnee yayi yaga yadda ta nutsu fuskar ta da wani irin yanayi na nuna  zaƙuwa tana kallon sa . Yawan ƙaunar da Amnee ke yiwa Rahima ya san kuskure kaɗan idan yayi kan lamarin nan zai matuƙar sanyata a ɓacin rai , shi yaya zai yi ne ? Muryar Khaalty Rahima da ta ratso shirun  wajen ya katse masa tunani ,   Da wani yanayi cikin muryar ta da ya sha banban da murmushin yaƙen da yake fuskar ta a lokacin tace ,   " Yaya , mun ji daɗi mun kuma yi farin-ciki da wannan haɗin da kayi niyyar yi , Sai dai Yaya , Hamza ai tuni ya riga ya zaɓi abokiyar zaman sa har kuma tafiyar su ta fara miƙawa cikin kwanciyar hankali da fahimtar juna ba tare da yana da niyyar  ƙara yin wani auren ba , dan haka ni ina ganin Yaya da dai an bar yarona ya zauna da matar sa ɗaya kar a ɗaura masa nawin mata har biyu da bai shirya ba . Prof da yake kallon duk su biyun , ya gyara zama , yana mayar da ganin sa gaba ɗaya kan Khaalty Rahima . " Rahima wannan ba hujja bace da zata hana auren Hamza da Aminatu , sai dai idan kin nuna min Aminatu ba ɗaya take da sauran 'ya'yan da na haifa da nake da ikon zaɓa musu abokan rayuwa ba, ko kuwa har yanzu baki huce daga abunda ya gabata ba shiyasa zaki gwada hakan ta hanyar hana wannan al'amarin tabbatuwa ko Rahima ? Da taruwar hawaye a idanun ta muryar ta cike da tashin hankali , ta shiga girgiza kanta tana cewa " Haram ko kusa ba haka bane Yaya , dan Allah kar kace haka , a tun kafin bayyanata Aminatu da ƴar uwarta suna da wani majiɓanci da ya wuce ka tsawon wannan shekarun ? kayi haƙuri ba nufina ba kenan , ni shi nake... "  idan ba haka bane to ki barni nayi abunda nake da manufar yi inshaAllah alheri ne a garemu baki ɗaya , Bai saurara ba ya juya ga Doctor hamza da zuwa lokacin gumi ke tsattsafo masa a goshi , da murya dake cike da gargaɗi Prof yace ,    " Likita kai nake saurare kai kuma me kace ?    Ɗago da kan sa yayi ya dubi iyayen sa , yanayin da ya gani a kan fuskokin su,  su duka biyu ya razana shi musamman ma Amnee dake masa wani kallo mai kama da harara , da sauri ya mayar da kansa ƙasa kafin muryarsa cikin rashin amo sosai ta fito ,        " Na'amince Baba , Na Amince Baa . Daga haka yayi shiru yana jin wani irin ɓacin-rai da ya taho masa tare da Amincewa auren yarinyar da ta gama yawon ta shekara da shekaru dan kawai tana ƴar uwar sa , Daga sama ya tsinkayo muryar Prof yana cigaba da cewa ,    " To Alhamdulillah Allah ya maka Albarka , ya baka 'ya'yan da zasu maka biyayya fiye da yadda ka min , Ubangiji Allah ya jiɓanci lamarin ka ya raba ka da sharrin duniya, Allah ya sa Albarka a zaman ku ya baku zuri'a masu yawa da Albarka , ka faranta min rai sosai . Ya nisa lokacin da Amnee wacce haƙoranta ke washe tana ƴar dariyar dake nuni da zallar farin-cikin da take ciki take amsa addu'o'in sa ya cigaba da cewa ,   " za'a haɗa auren naku da na Rahima ayi shi duk a rana ɗaya dan a rage hidima idan ya so ko bayan sati guda ne idan ka samar mata muhallin da ya dace da ta zauna a can Abujan kusa da kai sai ka taho ka ɗauke ta hakan yayi ko ?   Yace yana mayar da ganin sa kan Amnee , wacce ta gyaɗa kai da sauri da maɗaukakin fara'a a fuskar ta tace , "Yayi sosai ma Baa Alaji , cikin sati uku masu zuwa ai su zainab sa iya zuwa Dubai yiwa takwarata kayan ɗaki . Da wani irin bahagon yanayi Doctor hamza ya ɗago yana kallon su , Khaalty Rahima da duk hankalinta ke kan sa ta yi gyaran murya kaɗan , cikin ƙanƙan da kai tace ,   "Yaa ka min izni nayi magana wannan karon a matsayina na innar ango madadin uwa ,    Murmushi Prof yayi , "An miki izni , yace " Yaya Dan Allah a mana alfarma , bayan an ɗaura auren a bamu ko da watanni biyu ne ya kammala shirin sa , kamar samar da wajen zama a tsanake , ya kuma sanar da uwargidan sa cikin kwanciyar rai ,  ya ɗan samu ya dai-daita lamuransa ,tunda nawi ne zai ƙaru masa kar a tsawwala yafi kyau yayi kome cikin lumana tunda indai ta zama matar sa ai kome ya kammala . Cike da amincewa Prof yace , " To shikenan tunda kun nemi wannan Alfarmar an muku , amma ya tabbar kafin cikar watanni biyun ya kammala duk wasu shirye-shirye tunda ɗan naki ai Babban likita ne albashin sa ya kai wani mizani amma duk da haka na ɗauke mar nawin sadaki da duk wasu hidindumu da suka shafi biki na shi hidimar shine ya samar mata da muhalli mai kyau tare da ɗaura aniyar kulawa da duk wasu hakoki nata da suke kan shi daga ranar da zata shiga gidan sa har zuwa ranar da mutuwa zata ɗauki ɗayan su , kaji ko ?   Ya ƙarasa zancen yana juya akalar tambayar sa ga Hamza ,   " Gyaɗa kai yayi nagode Baa Allah ya ƙara girma ya furta hakan yana miƙewa yayi hanyar ficewa daga falon , Khaalty Rahima ma godiyar tayi musu sosai kamar zata zubda ƙwalla dan farin-cikin gatan da ake shirin yiwa ƴar ta , Tafe yake baya sanin ina yake ajiye ƙafar sa ,  Jacket ɗin sa riƙe a hannun sa saboda zafi da yake ji yana damunsa kota'ina cikin jikin sa tsabar tashin hankali , abunda ya faru yanzu a falon Baa so yake ace wani rarraunan mafarki ne daga cikin jerin shuɗaɗɗun mafarkan da ya dunga yi a shekarun baya , domin tuntuni ya wanke tabbatuwa hakan daga zuciya da tunanin sa . Har ya kusa sashin sa ya tsinkayo muryar Khaalty Rahima tana ƙiran sa , juyowa yayi yana ƙirkiro wani rarraunan murmushi ya ɗora a fuskar sa ,   Ta ƙaraso idanun ta akan fuskar sa tana nazarin sa , muryar ta cike da nutsuwa tace    " Hamza kada fa ka damu kan ka wajen yin duk wasu hidindimu ko da gidan da zata zauna ɗin ma ka kama muku mai sauƙi idan ma ba hali ko ɗaki guda sai a bata a cikin gidan da kuke zaune nasan 'yata safiya ba zata ƙi ba , idan kuma duk hakan bata samu ba , zan sa Ukhtee ta roƙi Yaya ko anan sashin naka na gidan nan ai sai a barta tayi zaman ta ba ma sai ta tafi can Abujan ba , shi zaman aure ai bautar Ubangiji ce wurin Mace da Namiji baki ɗaya .   Tausayin ta ya kama shi , bai bar murmushin da yake yi ba yace " kar ki damu Khaalty yadda duk Baa ya ce haka za'a yi inshaAllah babu abunda zai gagara ,   Murmushi tayi , sannan ta cigaba da cewa , "Nagode, Nagode , yadda ka rufa min asiri kaima Allah ya rufa maka, ya baka 'ya'yan da zasu maka fiye da abunda kayi ga iyayen ka , nagode nag... Hannunta ya riƙo ," haba Khaalty godiyar me kike min haka , ai ni...   Da sauri ta katse shi , tana cewa "Godiyar kome ma , ka yi kome da yakamata nayi ta gode ma Hamza Allah ya ma Albarka ,   " Amin ya amsa yana sakin hannun ta ya juya ya nufi sashin sa , A hanya komawa ciki Khaalty Rahima da Amnee suka haɗu , cike da farin-ciki suka rungume juna ba sai bakunan su sun furtawa junan su ba babu makawa sun san zucoyoyin su cike suke da farin-cikin faruwar wannan lamari. " Baa Alaji yace a tambayi takwarata ita ma, ko ta amince ? Ko kuwa tana da wani wanda take so ya shirya yin aure , dan fa ba za'a mata dole ba , Ɗaure fuska Khaalty Rahima tayi , " wanne irin ma a nemi amincewar ta Ukhtee ? Shi namiji ma aka masa dole bare ita mace ?ai koma waye take so dole ta haƙura tunda Yaya ya yanke hukunci . Murmushi Amnee tayi , " wa yace miki dole aka yiwa ɗan ki ? Ba soyayya bace ya sa ya ɗauko ta ya kawo ta gidan nan lokacin ma bai san ko suwaye su ba ? Ai kawai dan dai kaddara ta gifta tsakani badan haka ba da auren su ma zaki gan su , Ƴar fara'a Khaalty Rahima tayi , " duk da haka Ukhtee kin san fa irin aibun da yake tare da takwarar taki , ni gani nayi kamar an tauye shi da aka liƙa masa auren ta , kuma a yadda ma na lura yanzu ɗan nawa baya yi da takwarar taki ko da a baya ya nuna ra'ayin sa akan ta , Wucewa gaba Amnee tayi tana cewa " koma menene dai idan aka yi auren ai sa shirya kan su , so na gaskiya ai baya kankaruwa sai dai wani abu ya dusashe tasirin sa , ni bari naje na samu takwarata na shawo kanta ta amince ayi abun nan ranta na so , ba zan so ba a takuramin ita da auren dole , Ƴar ajiyar zuciya Khaalty Rahima tayi tana murmushi ta bi bayan Amnee zuciyar ta cike taf da ƙauna tare da farin-ciki marar misaltuwa da rabon ta da irin sa shekarun dayawa . *** A ɗaki Amnee ta tarar da su ukun suna gwada ɗinkunan su , Falmata tana mitar burguza-burguzan riguna da siket ɗin da telan ya yi mata , " mai sunan Mama dan Allah ki ga wannan siket ɗin yadda ya min yawa ba ko fasali ni ɗai gaskiya a mayar ya rage min , naku ke da Yakaka cas-cas irin na ƴan mata amma ni shine ya min haka siket kamar buhu ?    Dariyar da tuntuni Yakaka take riƙewa ita ta ɓurtso kanta , cikin dariyar take cewa ,    " Kai Falmata gaskiya ba'a iyar miki , ke kome aka miki bai yi ba, yanzu da matsattsu aka miki cewa za ki yi sun matse ki sun hana Baby sakewa yanzu kuma anyi wanda Baby zai wataya kince an miki buhu , Allah kana gani dai ,  ka shirya min Falmata ,    " zunɓuro baki Falmata tayi dai-dai da shigowar Amnee da Mamar su ,    " Maama kin ga ku faɗa musu su daina tsokana ta kullum Rahima da Yakaka basu da abun yi sai tsokana ta, yanzu ku ga irin ɗinki da suka kai aka min , ta ɗaga siket ɗin ta , "ku ga kuma nasu , tace tana ɗaukar siket ɗin Yakaka ta nuno , ta ɗora da cewa  " dan Allah Amnee za'a ce tela ɗaya ya ɗinka ? Nawa kamar wata gani garau , nasu kuma na yayi ?   Karɓar kayan Amnee tayi tana ajiyesu gefe , tace " sun yi girma kam , kiyi haƙuri za'a mayar ya rage miki wannan ɗinki ai ko a Niger ayi wanda ya fi shi tsari bare anan Nigeria gidan cancara ɗinki , Ganin ta ta mayar kan Yakaka da take kallon su tana dariya da haƙori ,    " Zo nan ki zauna takwara ta magana nake tafe da ita mai muhimmanci , duk ku nutsu ku bar shirmen nan ,   Amne ta furta hakan lokacin da take zama a bakin gadon , tana yiwa Yakaka nuni da gefen ta kusa . A nutse Yakaka ta taho kusa da ƙafafun Amnee ta zauna a ƙasa maimakon gefen ta da ta nuna mata , Cikin nazari Amnee tace ,    "  Takwara akwai wanda kuke tare ne ? Ina nufin akwai wanda kuka yi wata magana ta aure da shi ?? Dumm Yakaka tayi , zuciyar ta na sauya bugu , a lokacin ba wanda ya faɗo mata sai wannan mutumin da yayi ta nacin bibiyar ta shekaru kusan biyu tana zille masa a abuja , kafin barinta Abuja dai Lubna tace ta ba shi number ta Amma ko sau ɗaya bata taɓa riskar ƙiran sa ba , wataƙila daman wasa yake , ita kuwa bayan shi ai ba wanda ta taɓa saurara mafi yawan masu cewa suna son ta duk gani take fasiƙanci zasu yi da ita , domin tunda tasan illar zina da zunubin ta take jin tsoron maza ma gaba ɗaya . Tunanin ta ya katse lokacin da taji Amnee na maimaita mata tambayar , a hankali ta girgiza kai , " Babu kowa Amnee ,     " kin tabbata ?  Ki fa faɗa min idan akwai ,   Amnee ta sake furta haka domin haƙaƙewa ,    Zuciyar Yakaka ta fara shiga ruɗu da son sanin dalilin da ya kawo wannan maganar ta sake cewa , " Allah babu kowa Amnee ,   " To Alhamdulillah , Aminatu kina jina ko ?   Bata jira ta amsa ba ta cigaba da cewa , " Baa Alaji , Baban ku na gidan nan ya yanke shawarar haɗa aure a tsakanin ku ke da Yayan ku Hamza , muna fatan ba za ki bijirewa Umarnin mu ba ?   A razane ta ɗago kan ta saboda yadda zancen ya zo mata baga-tatan , ta shiga raba ganin ta tsakanin Mamar su da Amnee cikin wani irin jirkitatcen yanayi , Ganin yadda fuskar ta ta nuna yasa Khaalty Rahima hanzarin tare ko wanne irin sakamakon da zai biyo baya ta hanyar cewa ,    " kuma har an riga an gama yanke magana za'a haɗa bikin ku rana guda da na takwarata nan da kwanaki goma sha biyu , babu sauran wata magana . Ihun da Rahima ta sa tana tsalle ta taho ta rungume Yakaka  shi ya katse zancen khaalty Rahima ,    " Alhamdulillah burin Big bro zai cika , Masha Allah Baa mun gode sosai wallahi , sai ta sake ta da gudu tana barin ɗakin tana cewa , " bari naje na taya bro murna wayyo Allah ,    Shiru ne ya ratsa ɗakin sai tashin sautin murmushin Falmata da farin-ciki mai tsanani ya bayyana kan sa a fuskar ta , " Takwara baki ce kome ba ? , Amnee ta sake katse shirun , A hankali Yakaka ta ɗago kan ta ta ɗan dubi Amnee muryar ta can ciki tace , " Shi ya yarda ?   Tambayar da ta karya zuciyar iyayen nata biyu har ma da Falmata , kafin Amnee ta amsa ta sake cewa , " Idan har shi ya yadda shikenan Amnee ni ai koyaushe mai muku biyayya ce Baa kuma nima Babana ne , nagode da duk abunda kuka min . Hannuwanta duk biyu Amnee ta sanya ta ɗago ta , ta zarce da rungumeta a jikinta ,   " Allah ya miki Albarka takwarata Allah ya baku 'ya'yan da zasu muku fiye da irin biyayyar da kuka yi mana , Addu'o'i ta cigaba da yi mata Falmata na amsawa da ƴar muryar ta dake bayyana amon murna , Miƙewa Amnee tayi tare da cewa ," bari naje na sake sabunta tsari da shiri bikin ya zama biyu , kai wannan shekarar ta zo min da ɗinbin Alheru Alhamdulillah Allah nagode ma , Bata jira cewar su ba ta fita ta bar su , su ukun ,    Yakaka ta ɗago idanunta dake cike da ƙwalla damuwa ɓaro-ɓaro a fuskar ta take kallon fuskar Mamar su tana son ko yaya ta bata damar da zata ce wani abu , A hankali Khaalty Rahima ta tako ta zauna a inda Amnee ta tashi , bata yadda sun haɗa ido ba tace " Naji daɗi da kika nuna halacci baki yi butulci ba , abu na gaba shine ki ɗauko haƙuri da juriya akan duk wani ƙalubale da za ki fuskanta a gaba ki riƙe su a matsayin makamin ki , sannan a ko'ina kika tsinci kan ki cikin kowanne hali ki ji tsoron Allah , Allah ya miki Albarka Amina .    " Amin,  Yakaka ta amsa hawayen idanun ta na sauƙa bisa ƙuncin ta , Miƙewa khaalty Rahima tayi saboda zuciyar ta ba zata juri ganin irin wannan damuwar mai tarin yawa da take hangowa daga Yakaka ba , abunda ta riga ta sani inshaAllah cikin auren nan nasu akwai alheri mai tarin yawa , Tasan abunda Yakaka take tsoro bai wuce illar dake tare da ita ba akan irin abunda ta aikata , ita ta ɗau hakan a matsayin kaddarar Yakaka, kuma inshaAllah a wannan gaɓar ta ƙudurci aniyar yakice kunya irin wacce iyaye mata ke nunawa ƴaƴan su , zata ɗauri ɗamarar gyara ɗiyar ta ciki da bai tare da mata darussa masu inganci cikin ɗan zaman da ya rage musu tare , da zai taimaka wajen sauƙaƙa mata duk wasu ƙalubalen da ka iya taso mata a gidan aure . Kayan gyara kuwa daga nan har N'Djamena, zata ɗau hanya ta tafi domin ta ga ta yiwa ƴar ta gyara mai kyau da zai taimaka ko kaɗan ne wajen samar mata da ɗan matsayi ko yaya a wajen Mijinta, sanin da tayi tana da abokiyar zama ko kusa ba zata so ƴar ta ta walaƙanta ba . ( Khaalty Rahima nima ina da saƙo zuwa N'Djamena nan amma ni turaren wuta nake so 🙄🤐 ) Tana bada baya daga ɗakin Falmata ta taso da sassarfa ta isa inda Yakaka take zaune kamar an dasa ta ko motsin kirki bata yi , tana zuwa ta rungume ta tana ƴar dariya-dariya tace , " Yakaka na Alhamdulillah , kin ga Al'amarin Allah ko ? Allah baya bacci Yakaka nayi murna , nayi murna , a kunne ta ta raɗa mata ,"Félicitations Mme Hamza Mustapha Dilmari, Kukan da tun-tuni ke cin Yakaka a rai shi ta saki lokacin da tashin hankali yayi nasarar lillisa zuciyar ta , " Aure ? Aure tsakanin ta da Doctor hamza mutumin da ya tsani kallon ko fuskar ta ?  mutumin da yake zargin ta da tafiya yawon banza ? Mijin sofi ƙawar samy Baby ? Anya Mamaa ba zasu kaita inda za'a kashe ta bane tun kwananta bai ƙare ba , a gareta wannan ba gata bane ba . **** Duk yadda Rahima ta dunga ƙwanƙwasa ƙofar falon Doctor Hamza bai taso ya buɗe ba duk kuwa da cewa yana zaune dirshan a ƙasa a falon sai dai damuwar da yake ciki ta toshe masa kunne daga jin hayaniyar Rahima , ya zurfafa cikin tunani .   Wani irin yanayi marar daɗi ya tsinci kansa a ciki , ko kusa da yasan abunda zai riska kenan a garin da bai zo ba , Yarinyar da ta gama yawon banzan ta bai sani ba ma ko ta maƙalo wata cutar ita ce dan kawai Baa yana son gyara wani shuɗaɗɗan kuskure sai ya laƙa masa auren ta ? Wannan da bata ajiye kome ba sai tarin ƙarairayi da yaudarar banza , har ita ce ake so ya gatata ? To wanne gata zai mata da bai nuna mata sumfurin sa ba a baya ? Shi ya sani a da ya so ta amma yanzu ko alama baya jin ɗigo na son ta sai ma baƙin-ciki da yake ji a duk lokacin da ya gan ta . Babu yadda zai yi , bashi da wata mafita shiyasa ya amsa auren ta da aka liƙa masa , da ace ba Khaalty Rahima bace uwar ta da Wallahi da ko ta halin ƙaka sai ya cisge wannan liƙin da ake son yi masa , To amma kasancewar ta 'ya ga Khaalty Rahima ya sa dole ya amince , zai aure ta , su zauna a yadda yanayi ya zo musu shi da ita ..! Assalamu Alaikum masu karatu Da fatan kun wuni lafiya ? Ina miƙo saƙon gaisuwa tare da fatan alheri agare ku baki ɗaya . To ga fa abun yazo , wai inji mai tsoron wanka , Ina nufin bikin Yakaka da Hamza 😂 sister J , da Raly Garba , ku ne fa masu rabon anko , sai dai kuma ga lokaci ya zo a ƙure kwana goma sha biyu kachal ai ya muku kaɗan. 🤔       [1/4, 12:40 PM] +234 816 886 5113: MAFARI ( HARGITSIN RAYUWA ) UMM'MUAZ 48 MAFI TSAWON DA BAI ZAMA KARSHE BA. A washegarin ranar da aka tabbatar masa da haɗin Auren sa da Yakaka nan da kwanaki goma sha ɗaya masu zuwa , Doctor Hamza ya tattara ya nasa ya nasa ya koma Abuja da sassafe , duk yadda Amnee ta dunga son shigo masa da zancen Yakaka tana son ta haɗa su , lokacin da ya shiga yi musu sallama ita da Baa , ƙi yayi , ko Khaalty Rahima sai ta wajen Amnee ya bar mata saƙon tafiyar sa . Gaba ɗaya baya cikin nutsuwar sa garin ya masa wani irin zafi . Prof da Amnee basu wani damu da yadda alamun ɗan nasu ya nuna dake bayyana bai yi farin-ciki da auren da ake shirin yi masa ba , suka cigaba da yin duk wasu tsare-tsare da shirye-shiryen yadda bikin zai kasance , an riga an buga katin auren Rahima har ma an rabar , ganin cewa bikin Hamza ba na farko bane ,na biyu ne ,ya kuma zo a ƙurarren lokaci , sannan abun nasu tuwona maina ne , saboda sune dangin uwa da na uba saboda a cikin baki ɗayan dangin Uban su Yakaka har yau an gaza samo ko guda duk kuwa da cewa sau uku Khaalty Rahima tana bin sansanin ƴan gudun Hijira ko Allah zai sa ta ci karo da wasu daga cikin tsirarun dangin Mahaifin su Yakaka duk kuwa da cewar tsawon zaman su ba zaman daɗi suka yi ba , saboda karan-tsana da suka ɗora mata ita da yaranta , haka siƙau , sai dai Allah bai sa ta gamu da ko wanda ya san su ba , kai ko mutanen ƙaramin garin nasu ma Allah bai haɗa ta da su ba . Dan haka sai basu wani damu da a sanar da dangi ba kawai suka bar lamarin a tsakanin su . Amne ta ƙarfafa da a rufe zancen auren a tsakanin su ne saboda tsoro da take yi kar danginsu suyi wani yunƙuri na hana auren sanin da tayi tun da can daman ba ƙaunar ta suke ba ita da Rahimar ta , tayaya kuwa zasu so 'yar Rahima ta auri Hamza ? musamman da ya kasance Hamzan ai tasu yake aure 'yar yar'uwar su . Dan haka ta dage akan a rufe zancen har sai ɗaurin auren ya matso a yadda ta so ma sai sanarwar ɗaurin auren kowa zai ji ,sai dai da alama hakan ba mai samuwa bane , koma menene ita dai zasu tsawaita addu'a ita da Khaalty Rahima kan Allah ya tabbatar da lamarin nan tare da Aminci Shiri suke sosai a tsakanin su , lokaci ne yanzu na wayar tafi da gidanka , da saƙo ke saurin isa inda ake buƙata , ta waya Amnee ta sanarwa da dangin su na can N'Djamena labarin bikin da ya zama uku ba ma biyu ba , watau Hamza ,Yakaka da kuma Rahima ƙarama . Murna ta ishe su a can nan take suma suka shiga sabunta shiri , da daman suke tsakiya da yin sa , saboda dayawa daga cikin su ,wannan karon suna shirin zuwa saboda su gana da ƴar uwar su wacce ta ɓace shekara da shekaru har aka fidda rai da sake ganin ta , Cikin masu zuwan har da yayun su maza da matayen su da wasu daga cikin 'ya'yan su , sai kuma dangin su na wajen uwa da na uba duk gasu nan dai gayya guda , Nan take labarin auren ya sake bazuwa a tsakanin su , jin cewa har da na 'yar Rahima mace da Hamza ɗan Aminatu, da za'a musu haɗin gida, nan take suka yi sabon zama na musamman , inda suka sake ninka gudummawar su da zasu tafi da shi da daman turaren wuta ne da turaren jiki na ruwa ( Humra ) har ma da na wanka da mayukan jiki da na gashi , ( kulaccan da karkar ) suka ɗau nawin yiwa Rahima ƙarama gudummawar sa ,a matsayin su na dangin uwa sai suka sake ninkawa da wani haɗin turaren wutar da humran , su kulaccan da karkar makamancin wanda yake ajiye duk suka haɗa acikin manyan mazubai suka rufe , Sannan suka sake ƙarawa da kayan ƙamsasa girki da daɗaɗa shi irin nasu na can , haɗi da ingantattun ganyayyaki haɗin shayi ( tea ) da suke ƙara lafiya da kuzari tare da sanya nishaɗi, shima roba-roba suka keɓence shi . Bayan haka matar baban wan su da ake ƙira Hajje khalsum ta ƙira Amnee tana sake tambayar ko akwai kuma wani abunda suke so a taho musu da shi daga nan N'Djamena ? Nan Amnee tayi amfani da wannan damar take sanar da ita buƙatar ta na son a haɗo mata kaya gyaran jiki tare da magagungunan mata ,irin nasu masu ɗauke da sunadaran da suke ƙamsasa kowanne saƙo na jikin duk wata matar da take amfani da shi , bayan sun mata gyara ciki da bai . Amnee ta cigaba da cewa a faɗa mata adadin kuɗin da zai isa a kawo kayan gyaran kashi uku , kafin ta gama bayani Hajje Khalsum ta katse ta , tana sanar da ita cewa ai wannan ta kawo cuta inda ake da tushen maganin ta , domin kuwa ƙanwar ta da suke uwa ɗaya uba ɗaya , ƙwararriya ce ta wannan fanni na gyaran mata ciki da waje , domin kuwa faɗin ƙasar su ansa da ingantattun magungunan ta , babban shago ne da ita anan babban birnin N'Djamena da taƙe sayar da irin waɗannan magungunan da kayan , har kuma ƙasa-da-ƙasa ake ɗaukar ta tana zuwa gyaran jikin , tare da haɗawa mata ingantattun magunguna dan haka kada ta damu , nan da kwanaki biyar inshaAllah zasu taho tare da ita . Zuciyar Khaalty Rahima ta daɗa cika da ƙaunar 'yar uwar ta , domin ko bata faɗa ba tasan cewa dan Yakaka ne Amnee ta ƙira Mai gyara , da daman tuntuni take son tayi wani yunƙuri akai , amma kunya da kara suka hana ta ganin cewa duk wasu ragamar bikin na hannun Amnee , sai kuwa ga shi zata sa a gyara mata Yakaka , Duk abunda ake na zafafa shirye-shirye , Yakaka ta maida kan ta mai zaman ɗaki , daga kuma ta samu sarari sai ta shige banɗaki taci kukan ta , tsoro da damuwa sun hana ta walwala , tuƙuru tsoron rayuwar da zata riska nan gaba kaɗan take , Daga Amnee har Khaalty Rahima ba wacce ta bata sarari bare ta ji damuwar ta saboda sun riga sun san ko damuwar ta mecece ?dan haka suka kyale ta suna sabgogin su , Ganin bata yin wani shiri , ko alamun gayyatar ƙawaye koda na mutunci ne yasa suka fara lallashin ta kan cewa " yakamata ita ma ta gayyaci mutane , ranar auren ta rana ce mai ɗimbin tarihi wacce yakamata mutanen da duk tayi ko da zaman mutunci da su ne su shaida wannan ranar , Yakaka tace " ita fa bata da ƙawaye , ƙawarta ɗaya Lubna kuma tayi aure , bayan ita bata da wata ƙawa , da suka matsa mata ma kuka ta sa tana cewa " Amnee Mama kun san fa irin rayuwar da muka yi , ina mutane suka mu'amalance mu da mutuntawa bare har su kai mu kusa da su ? Da zamu iya ɗorar da zumunci idan bayan Malama Maryam da Lubna babu wasu mutane ta wajena , sai ta basu tausayi suka bar maganar , amma daga baya sai suka sa ta ƙira Malama Maryam ,bayan sun gaisa ta miƙawa Amnee wayar dan ita kunya take ji ta faɗi ranar auren ta da kanta , ta baki da baki Amnee ta shaida mata sanya ranar bikin 'yar ta kuma ɗalibar ta , Ba ƙaramar murna Malama Maryam tayi ba har ma tayi Alƙawarin halartar bikin , basu bi ta kan Yakaka ba wacce take faman ƙwalan-ƙwalan da ido tana son sake yin wani kukan , suka yi ficewar su daga ɗakin suka bar ta , dumuwar ba zai sa a fasa kome ba , domin na ɗan lokaci ne kuma gata ne babba ake shirin yi mata . Cikin kwanakin nan Falmata sai ta fita walwala , domin ita labarin bikin Yakaka da Yaya dakta yayi awo gaba da kaso kusan talatin na damuwar ta , duk da cewa ba wai ta daina jin damuwa da rashin ji daga Biyamuradi bane , farin-cikin auren Yakaka ne yake saisaita mata damuwar ta . Doctor Hamza kuwa tun ranar da ya isa Abuja ya so sanarwa da Sofiya halin da ake ciki kan lamarin aure da ya taso masa , saboda hakkin ta da yake kan sa ya zama dole ya sanar da ita . Sai dai yadda ta tare shi cike da ɗoki kamar wanda ya shekara rabon sa da ita ba kwana guda ɗaya tal ba , sai ya kashe masa ƙwarin guiwar sanar da ita labarin da yake tafe da shi sanin da yayi ba abun farin-ciki bane a wajen ta, Sai yayi zaune kawai yana bin ta da kallon yadda take ta ririta shi tana tarairayar sa , tayi kwalliyar ta fes-fes cikin riga da siket , ta mammatse manyan kayan da yafi so tare da ita sun firfito ko yaya ta motsa suna rangaji tare da dusashe masa ƙarfin gani suna tayar masa da kwaɗayi . Shi dan ta shi tuni ya haƙura da ya zauna tare da ita ,ita kaɗai saboda a halin zaman su na aure babu ta inda ta kuskuro shi sai ta wajen girki wanda shi kuma hakan bai wani dame shi ba saboda shekarun girma da ya fara shigo masa , a matsayin sa na likita shekara arba'in ya kamata ya fara kiyaye kansa daga ciye-ciye barkatai da sunan jin daɗi . Rashin haihuwar su kaɗai ke ɗan taɓa ransa , kuma yayi-yayi da ita taje asibiti ya haɗa ta da kwararrun likitocin mata su duba ta taƙi , daga baya yayi watsi da ita lokacin da ya fahimci akwai wata matsala tata da take ɓoye masa , koma menene ita ta sani shi dai ya san lafiyar sa rass , domin a farko-farkon shekarun auren su yayi gwaje-gwaje da dama kan rashin haihuwar su domin gano ina matsalar take ? Ta haka suka tabbatar masa da ingancin lafiyar ƙwayayen halittar sa dan haka shi bashi da fargaban kome , Yawan ƙaunar da take gwada masa salo-salo yasa yake ɗaga mata kafa , domin kuwa ta san ta kan sa sosai bai wani cika murɗe mata ba muddin ta raɓu da jikin sa , Domin a yanzu ma kasa sanar da ita labarin ƙarin auren sa yayi , maimakon haka kawai sai ya ɓige da neman samun nutsuwar gangar jikin sa ya shiga shinshinata yana gwada mata soyayya irin wacce ita dai tunda take da shi bai taɓa yi mata makamancin haka ba , zuciyar ta ta ji ta kunburo tana daɗa tunbatsa da ƙaunar sa , gefe guda kuma wani irin tsantsar farin-ciki take ciki , "yau Doctor ne yake nuna mata zallar so tare da kalamai masu tausasa zuciyar masoyi ? Babu shakka masu iya magana suna cewa daɗewa a mabauta ma ƴanci ce ." Shi kuwa a ɓangaren sa zuwa washegari ya tabbatar dai ba zai fa iya sanar da ita ba , sai ya kuɗurce zai tura ta can Maiduguri da wuri , su da suka rakito auren sa san yadda zasu yi su sanar da ita domin shi Allah ya sani ba zai iya ƙarawa kansa damuwar haukar da sofiya zata iya yi ba akan ta shi damuwar da yake ciki , gara tayi haukar ta acan idan yaso ma ta huce akan ita Yakaka , shi duk wannan ba damuwar sa bace tsuntsun da ya jaa ruwa . Saɓanin yadda ya zaci damuwar sa zata zama ƙanƙanuwa sai lamarin ya zarce tunanin sa domin tunda aka yi batun auren su kullum tsaffin laifukan ta daɗa sabunta kan su suke a zuciyar sa , baki ɗaya sai ya susuce kamar farkon lamarin . Ya zama ko office ya tafi baya wani taɓuka aikin kirki , har waɗanda ke tare da shi suka fara fahimta , Suleiman Amininsa shine ya fara farga da yawan damuwar da yake ciki ya kuma matsa masa da tambaya ? a farko Doctor Hamza ba shi da niyyar sanar da Suleiman da kan sa , sai ko bayan auren , sai dai yadda ya matsa masa da tambaya yana nuna damuwar sa a fili ya sa shi sanar da shi cewa "aure zai ƙara da ƴar Innar sa da aka ba shi , " Wani sasakai Doctor suleiman yayi yana kallon Hamza , kafin ya wani kwashe da dariya , sai da yayi dariyar ta ishe shi , Doctor Hamza bai ce masa ƙala ba illa ma rubuce-rubucen sa da ya shiga yi , yana jin yadda ransa ke ɓaci da dariyar walaƙanci da suleiman ya sanya shi a gaba yana yi . " Ka ce dai alƙadarin Safiya ya karye , zaka yi wani yunƙuri dan ganin ka fara tara naka zuri'ar , lamari yayi kyau haka ake son Namiji to amma nayi mamaki ina kuma kan yi ko yaya zaka yi da mata biyu ? Da wutsiyar ido Doctor hamza ya dube shi , ba tare da ya bar abunda yake yi ba yace , " Su masu mata biyun me suke yi da na su ? Wata dariyar Doctor Suleiman ya sake kwashewa da ita kafin ya ɗora da cewa , " wataƙila jera su suke suna ado da su a gidajen su , ya ɗora da cewa watanni nawa aka sa lokacin bikin ? Banda abunka abokina to menene abun damuwa ? Ai hurhuɗu ya kamata ma mu ajiye , domin ko nima ba domin tafiyar nan da na ɗan yi ba da yanzu batun auren mu yayi nisa da Aminah ta , wataƙila ma sai dai mu haɗa ayi rana ɗaya tunda kuwa ita ma ƴar Maidugurin ce , wata nawa aka sa ? Muryar Doctor Hamza can ƙasa yace , " kwanaki goma kachal suka rage har da yau da muke ciki , Tsumu Doctor Suleiman yayi yana kallon sa wannan karon kamar bai yadda da abunda yace ba , ganin haka yasa Doctor Hamza cigaba da cewa , " tare za'a haɗa da na ƙanwata Rahima , saboda ayi a huta , tarewar kuma sai yadda hali ya min wataƙila ta kai watanni huɗu a maidugurin ko ma fiye da haka kasan dai kome daki-daki ake yin sa . Da fara'a sosai a fuskar sa Doctor Suleiman ya shiga taya shi murna yana taya sa shi da fatan alheri cikin raha ya ɗora da tsokanar sa , " kace ciwon so kake ciki mana tare da kewa , shiyasa duk ka wani zama haka , babu shakka wannan ƙanwar tamu mai sa'a ce , to sabon shiri kenan zamu fara dan angwanci ya same mu da rana tsaka ba tare da mun shirya ba , amma duk da haka ma ɗan yi wasu tsare-tsare a gurguje me da me za'a yi na biki ? Kallo mai kama da harara Doctor Hamza ya masa , kafin yace " Dan Allah zan roƙe ka Alfarma Suleiman, kar ka ƙara min damuwa , duk garin nan bayan kai ba wanda na faɗawa zancen nan , ko ita sofiya bata san da zancen ba dan haka ka ma bar maganar wani biki zancen ya tsaya kawai a tsakanin mu , bayan kai da daman zaka je bikin Rahima babu wanda zan gayyata . Da wani irin yanayi Suleiman ya dube shi kafin yace " ko meyasa ? " kawai ra'ayina ne , mu ba yara bane da za'a yi wani raye-rayen biki ina ma muka ga lokutan ɓatawa ?. Gƴaɗa kai Suleiman yayi cike da shakku yace " to shikenan tunda kace haka Allah ya kyauta . " Amin nagode abokina , Doctor Hamza ya amsa masa , domin ya sauƙaƙa yanayin rashin daɗi da ya hango a tare da Suleiman sai yace , " ina aka kwana kan batun lamarin ita Aminar taka ? ko idan muka je Maidugurin za'a yi wani motsi mai ƙarfi ne ? kasan fa kun jima da yarinyar nan ya ci ace anyi auren nan . Cike da zaƙuwar jin an masa susa inda ke mar ƙaiƙayi Doctor Suleiman yace ," bari kawai abokina wannan yarinyar ko yau aka kawota gidana ta walashe ni , gyara zancen nan ka ma , saboda ai ni na jima ina son ta ba wai mun jima a tare ba , domin kuwa ai ita har yau bata wani bani dama ba , ni kaɗai ke fama , Ya dubi fuskar Doctor hamza da yayi kasaƙe cike da takaicin yadda ya zauna gotai-gotai da shi 'yar yarinya ƙanƙanuwa na masa yawo da hankali wajen shekaru uku , sai kace ƴa gwal ? Doctor Suleiman ya katse zancen da Doctor Hamza yake son ɗorawa ta hanyar cigaba da cewa , " kar ka ga laifina Abokina , Amina ta cancani da kowanne ɗa Namiji yayi sha'awar ajiye mace mai nagartartun halaye da Addini haɗi da nutsuwa irin ta , wallahi ko kai da kan ka idan na baka labarin irin rayuwar da yarinyar take yi mai cike da tsantsanin kiyaye kan ta duk kuwa da cewa inda take rayuwa ƙazamtatce ne , halayyanta na ƙwarai nake kwaɗayi ba kome ba , saboda na sha gwada ta ba sau ɗaya ba , na kuma sa mutane wasu daban ma sun gwada ta amma ko sau ɗaya ban taɓa kamata da wani laifi saɓanin zahirin ta da take bayyane kullum cikin kamala da nutsuwa ba . a yadda kake ƙyamatar halayen wasu matan nasan zaka yi mamakin nagartar da ita take da shi , kuma zaka bada goyan baya ɗari bisa ɗari akan na auro ta , musamman idan ka ji irin hali na tausayawa da suka riski kan su a ciki ita da ƴar uwar ta , Cike da gajiya da yadda ya zauna yana yabon wata wacce har yau shi da kan sa bata bashi darajar da za ta saurare shi ba , bare kuma su abokan sa Doctor Hamza yace " to Allah ya tabbatar da Alheri abokina . Kamar yadda suka yi alƙawari ana saura kwanaki biyar ɗaurin Aure Mutanen N'Djamena suka iso ,sun tasamma mutane ishirin da ɗoriya , domin sun kusan cika falon Prof da anan suka fara ssuƙa , bayan an gaisa murnar sake ganin juna ta kachame a tsakanin su har da 'yan koke-koke , banda yaren su na larabaccin Chad babu abunda ke tashi a wajen , Zainab , Hafsa da suka iso tun jiya , har Rahima haɗi da Yakaka da Falmata , a tsakanin su duk babu wani mai jin yaren har sosai , dan haka sai suka tsaya kallon su fuskokin su ɗauke da murmushi , Bayan sun ɗan nutsu sun sha ruwa da lemu , sai Matan suka shiga ciki inda za'a musu masauƙi , Mazan kuma suka tsaya anan Sashin Prof . A ciki Amnee ta sake gabatar da Yakaka da Falmata , nan aka fara rungumar su ana sumbatar kumatun su da goshi , cike da nuna zallar ƙauna , daga baya kuma aka sake sabuwar gaisuwa har da su Hafsa da mafi yawa sun riga sun san su , su Yakaka ne baƙi . Ba'a kwana ba Hajje Nadiya tare da tawagar ta mata huɗu da ta taho da su domin su taya ta suka buƙaci da su fara aikin da ya kawo su na gyaran Amare . Tun ana saura kwanaki biyu ɗaurin Aure Sofiya ta iso Maiduguri , amma sai ta ƙi ƙarasawa gidan su Doctor Hamza tayi zaman ta a gidan su tare da Mamar ta Hajja kori , da ita ta zuga ta tace tayi zaman ta sai ana gobe ɗaurin auren da Yamma sai su tafi tare , ba dan kome ba kuwa sai dan rashin shirin da yake tsakanin su da Amnee da Khaalty Rahima . Da ko kusa basu so Auren Amnee da yayan su ya sake ƙulluwa ba , kuma duk yadda suka so hana tabbatuwar lamarin fir Prof yaƙi saurarar su , ita kanta zuwan ta wajen sa biyu da zummar yi masa famfo amma bata samun fuska dan haka ta haƙura . Babu abunda yafi ƙara basu haushi irin dawowar Khaalty Rahima da suka fi tsana gidan wannan karon har ma da marayun 'ya'yan ta kamar yadda labari ya iske su Dan haka suka tsara zasu janye jikin su daga sabgar gidan sosai , sai ranar juma'a da Yamma lis , ana tsakiyar yin sakun lallen Amare tukun suka iso , ba su kaɗai bane ƙungiya suka yi da ɗan yawan su domin baki ɗayan ƙannen Prof matan sai yanzu suka zo tare da wasu daga cikin ya'yan su mata , sauran dangi kuwa mafi yawa sai gobe zasu zo . kai tsaye iyayen suka yiwa sashin Prof tsinke ba tare da sun bi ta kan jama'ar sauran Jama'ar Amnee ba mutanen N'Djamena da su Malama Maryam wacce ta iso jiya da Yamma . Suma kuma basu kula su ba , suka cigaba da gudanar da sakun lallen da aka tsara shi cikin irin Al'adun su na mutanen Chad , Kota'ina ƙamshin turaren wuta ne ke tashi da ake zuba shi ta kowacce kusurwa na filin wajen , haka Sofiya tare da wasu daga cikin yaran mata 'yan uwansu suka ratsa taro zuwa ainahin inda amaryar take zaune Abunda ya ɗaure musu kai bai wuce ganin Amaren su biyu ba tare da wacce su sauran basu kai ga sanin ko wacece ba ? ko ita Sofi sai da ta bar yatsine-yatsinen da take yi ta nutsu sosai tukun ta iya shaida Farar balarabiyar da take zaune daga gefen Rahima da aka musu ado iri ɗaya cikin jar lafaya , tundaga kan su har wuya da hannuwa zuwa ƙafafun su adon sarƙoƙi ne masu ruwan gwal irin wanda shuwa arab ke adon bikin su da shi , ( baki ɗayan kayan gudummawa ne daga Hajje Khalsum ) Muƙut ,! Sofiya ta haɗiye busasshen yawun da ya mata saura a baki , kafin ta ɗora da ɗan siririn tsakin da ya bayyana fili . Da ɗan sauri ta matsa kusa da Hafsa zuciyar ta na ƙara ƙarfin bugun da bata san dalili ba , " kamar nasan wannan kuma Bikin biyu ne wai ? Ta ce tana nuno Yakaka a walaƙance , Murmushin yaƙe Hafsa tayi sannan tace " ƙanwar mu ce 'yar Auntien mu Rahima , Da sauri ta sake cewa , " Ok daman wannan yarinyar ita ce ƙanwar taku da aka ce an tsinto su ? Kuma bikin ta itan ma ake yi na gan ta anan kusa da Amarya ko duk shisshigi ne da cusa kai ya bawan gado ? Wata daga cikin ƴar dangin su da ta zo ta jaa hannun Hafsa ɗin tana bata saƙon Amnee na ƙiran ta , ita ta hutatce Hafsa daga bada Amsar da take ƙoƙarin harhaɗowa cike da zullumi . Zare hannuwanta tayi daga cikin na Sofiya ta bar ta nan a tsaye , Ji tayi sam ba zata iya tsayuwa a wajen ba tana kallon Yakaka wacce sai ƙirƙiro ƴar fara'a take a tsakanin ƙawayen Rahima da suka zama kamar nata sai zuwa suke ana yin hoto , tare da yi mata fatan Alheri Bata sake bi ta kan kowa ba ta zare jiki ta nufi sashin Amnee inda ta tarar ba yawaitar mutane a falon , mutane basu wuce huɗu ba ƙawayen Amnee , kai tsaye ta nufi ɗakin Amnee da take jiyo muryoyin su daga ciki , Amnee da Khaalty Rahima haɗi da Hajje Khalsum duk shiru suka yi daga tattaunawar da suke suka bita da kallon ganin yadda ta shigo musu ɗaki bagatatan babu neman izni . samun waje tayi ta zauna kafin ta fara gaishe da Amnee , da ƴar fara'a Amnee ta amsa , daga haka shiru tayi tana latse-latsen waya bata da niyyar gaishe da sauran mutanen , dan haka fuskar Amnee ta ɗan sauya daga fara'ar da take tace , " Safiyya baki ga 'yan uwa na bane ? Wannan ƙanwata ce wannan kuma matar wana maza ki gaishe su . Yanayin ta na bayyana rashin jin daɗin yadda Amnee ta disga ta a gaban mutane kamar wacce aka toshewa baki tace " Sannun ku ina wuni ? Fuskar Khaalty Rahima ɗauke da murmushi sosai ta amsa mata har tana ƙarawa da tambayar ta Mamar ta ? Bata bata amsa ba ta mayar da kan ta ga fuskar wayar ta , Sun cigaba da tattauna yadda wasu al'amuran da suka shafi bikin zasu kasance , kafin su tsinkayo muryar Hajja kori da take ƙwalawa Amnee ƙira tundaga ƙofar falo , A kusan tare suka miƙe da sofi wacce ita ma tashin hankalin da ta ji a muryar Mamar ta ya firgita ta , Suka fito falon a tare kichiɓus suka yi da tawagar su Hajja kori tare da sauran ƴan uwan su na kurkusa da suka zo tare , Kamar zata cukumo Amnee haka ta tsaya a gaban ta tana huci , sannan tace " Amina baza ki taɓa sauyawa daga mummunar zuciyar ki mai cike da baƙin-hali ba ke da wannan Annamimiyar ƙanwar taki , da daga dawowar ku ke da ita shine kuka haɗa kai kuka maƙalawa ɗan mu auren Shegiyar ƴar da .... A tsawace Amnee ta katse ta bayan ta matsa baya kaɗan tace , "Hajja kori ki dakata , ya isa kar ki sake ki ce za ki tozartani ko ki tozartamin 'yar uwa ta , wanda kuka yi a da can ma ya isa wannan masifar taku da bala'in a yanzu bazan ɗauke shi ba domin kuwa kunne ya sake ƙaho ya girma . aure kuma tsakanin Yakaka da Hamza babu wanda ya isa ya hana ƙulluwar sa muddin ni na tsugunna na haifi Ɗana nayi ɗawainiyar sa sai ya auri Amina Yakaka , idan kuma a wannan karon ma za ku hana ne to Bismillah sai mu gani . Ƙara matsowa Hajja kori tayi jikinta har tsuma yake tace " tsohuwar kilaki haka kika ce ? Babu shakka dole kice ƙaho ya girma saboda kin gama yawon banzan ki a bariki kin dawo za ki laƙawa.... " Momy kori ki saurara haka nan Dan Allah duk abunda za kiyi kada ki aibata min uwa da mummunan ƙazafi , Muryar Doctor Hamza a kausashe ta ratso falon wanda sauƙar sa kenan a garin ya nufo gida yana faka motar sa bai ko gama tsayawa ba Hafsa ta ƙira shi hankalin ta a tashe tana shaida masa rigimar da ƴan uwan Baa suka zo su nayi musu . Cikin takun sa na nutsuwa ya ƙaraso wajen , yana zuwa ya shiga tsakanin su yana fuskantar Amnee , hannuwan sa duk biyu yasa ya dafa kafaɗun ta , cikin kwantatciyar muryarsa marar amo yace , " khaalas Amnee , Dan Allah kar kiyi hayaniya ki bawa kan ki stress kiyi haƙuri kin ji ? Ganin ta ta sauƙe akan sa idanun ta cike da ƙwallar ɓacin rai , jin irin mummunan ƙazafin da Hajja kori ta yi mata a gaban jama'a , zata yi magana ya katse ta " Kiyi haƙuri Ummii mu je ki huta . Hajja kori wacce ta ƙulu da yadda ya juya mata ƙeya yana rarrashin uwar sa alhalin ita tudu biyu take ci a wajen sa na babar sa kuma surukar sa , a fusace tace " Kai Hamza ƙaramin marar kunya munafikin maza , tare da kai watau aka haɗa baki aka munafunce mu kana sane , watau kai gaka mai uwa ko ? To ka tabbatar da cewa sai ka zaɓa tsakanin 'yata da wannan koɗaɗɗiyar shegiyar yarinyar da ake shirin aura maka , ƴar da ba'a san asalinta ba . Bai juyo ba , yace " Momy kori kema kiyi haƙuri Dan Allah . "Amnee mu tafi ɗaki ki huta , yace yana juya kafaɗun ta suka fara taku , " Doctor , Chak ya tsaya lokacin da sautin muryar Sofiya ya doki kunnuwan sa ,da sassarfa kamar ana tunkuɗa ta ta ƙaraso ta zagayo ta gaban su , idon ta da suka firfito da ke bayyana tsantsar firgicin da zuciyar ta take ciki ta tsattsare sa da su , cikin wata irin murya tace " Da gaske za ka ƙara aure ? Kai ne za ka auri yarinyar nan Yakaka ? kuma wai gobe ne auren naku ? Ganin sa ya kai kan Amnee da take raba ganin ta a tsakanin su , fuskar ta na bayyana ciwon da ran ta ke ciki, muryar sa can ƙasa yace " Gaskiya ne Amma ki bar maganar nan daga baya zamu yi . Kewaye ta yayi suka wuce cikin ɗaki , Ukhtee Rahima da take tsaye daga bakin ƙofar ɗakin idanun ta cike da ƙwallar tuno da wata rana mai kama da wannan a cikin wannan falon lamari mai muni ya haka ya faru ta silar dangin Prof da sanadin haka ne rayuwar su ita da 'ya'yan da ta haifa suka faɗa a garari , sai ga shi a yau tarihi yana sake maimaita kan sa sun kuma gwada hakan akan 'yar ta, daga ƙasan ranta take tambayar kanta wai laifin me ta musu ne da suka tsane ta , tsana mai muni ya haka ? Juyawa tayi ta rufa musu baya suka rufo ƙofar . Wani irin zaman 'yan dabaro Sofiya tayi a ƙasa dirshan kafin ta ƙwala wani irin ihun da yasa Rahima da Yakaka hanzarin ƙarasa shigowa falon da suke daf da ƙarasowa daman . " Ƙarya ne , inaa no no wallahi ƙarya ne , Doctor baka isa ka min haka ba , Momy kice mafarki nake dan Allah ? Ta ƙarasa sambatun da take tana miƙawa Momy kori hannu daga inda take kamar 'yar yayen da take son uwar ta ta ɗauke ta, A fusace Momy kori ta ƙaraso wajen , ta fara jaan hannun ta tana ƙoƙarin ɗaga ta , bakin ta har kumfa yake lokacin da take cewa , " sai ki tashi mu tafi ai shugabar 'yan taurin kai marar zuciya , tun farko ai na faɗa miki akwai ranar ƙin dillaci muddin kika yadda kika auri ɗan wannan Annamimiyar matar , amma da yake kafiya ce da ke kika nace kika liƙe masa kika ƙi kowa kika zauna zaman jiransa shekara da shekaru . "to ai ga shi nan kin fara gani kishiyar rana tsaka ,baki da ko darajar da za'a sanar dake bare a miki abunda ake yiwa mata a al'adance idan aka tashi musu kishiya , idan baki bar gindin auren ɗan Amina ba kaɗan ma kika fara gani daga cikin irin ƙiyayyar da zata zuba miki , A haukace Sofiya ta warce hannun ta daga cikin na Momy kori , da ƙaraji a muryar ta tace , " ki bar ni Momy , nace ki bar ni wayyo Allah na na shiga uku Doctor meyasa za ka min haka duk irin kula da son da nake nuna maka irin sakayyar da za ka min kenan ? Wani mummunan tsaki Momy kori ta jaa a fusaace tace , " to kar ki tashi dan uban ubanki ki zauna kina kuka anan , kina sambatun wofi akan wani lusarin yaron da bashi da zaɓin kan sa , shegiya mahaukaciya zauna anan nace , Daga haka ta fice a fusace , wasu daga cikin dangi da suke 'yan kanzagin ta suka rufa mata baya , wasu kuma duuu suka yi kan sofiya wacce take ta rafsa ihu kamar wacce uwar ta da ubanta suka mutu a haɗarin mota . Yakaka wacce duk haukar da Sofiya take yi tana kallon ta , a hankali ta fara jaan ƙafafun ta tana yin baya-baya zuciyar ta kuwa cike da tsoron kar Sofiya ta gan ta , Ai kuwa bata yi nasara ba domin kamar ancewa Sofiya ɗago kan ki karaf ta sauke idanunta akan Yakaka , Wata irin zabura tayi ta miƙe har tana ture matan da suka taru suna rarrashin ta dayawa daga cikin su rayukan su a ɓace yake da irin cin zarafin da suke ganin an yiwa 'yar uwar su , yi mata kishiya ba tare da an sanar da ita ba , sai a wajen bikin ta samu labari babu shakka a wajen mata wannan shine iyakar cin zarafin da ɗa Namiji zai iya yi musu . Kukan kura tayi ta kaiwa Yakaka cafka , da gudu Yakaka ta kewaya ta bayan kujeru tayi ɗakin Amnee dai-dai da murɗo ƙofar da Doctor Hamza yayi ya fito daga ɗakin , Tana zuwa ta shige jikin sa ta ƙanƙame shi , a bazata ya ji shigar sa jikin sa , dan haka ya ɗago kai a firgice dai-dai tahowar Sofiya , a cikin ƙanƙanin lokaci ƙwaƙwalwar sa ta fahimci abunda ke faruwa dan haka ya juya baya da sauri , dukan da Sofiya ta kawo gami da chafkar da taso yiwa maƙogoron Yakaka ya sauƙa a bayan sa , Tun ƙarfinta ta shiga dukan bayan sa da ya yiwa Yakaka rumfa da shi , tana ɗura ashar tare da shan alwashin a kan sai ta kashe Yakaka , Da kyar ya ɓanɓare Yakaka daga jikin sa wacce ta shige masa jiki ta runtse ido gam zuciyar ta bayan bugu ba abinda take yi , addu'o'i iri-iri bata gama wata take kama wata . Ƙofar ɗakin Amnee ta murɗo ta leƙo , lokacin da yake zare Yakaka daga jikin sa , " Menene kuma hakan ? Amnee ta tambaya a tsawace , Yakaka tana jin muryar ta ta juya da gudu ta kutsa ta bayan ta ta tsaya tana kallon Sofiya , tsintar kan ta tayi da kwashewa da irin dariyar nan ta na tsira , da kuma ƙarin ganin yadda Makeup ɗin da Sofi tayi duk ya mata muzu-muzu a fuska ya kwaɓe mata , kamar wata dodo . Ganin Amnee bai sa Sofiya ta bar zage-zagen da take yi ba , sai ma daɗa zabura da take yi tana son kamo Yakaka , wacce har lokacin dariya take yi da gajerun fararen haƙoran ta , Dariyar ta ta shagaltar da Doctor Hamza wanda yake ta faman rirriƙe Sofiya kamar wata tunkiyar da take rawar turke , fuskar sa da ɓoyayyen murmushin da ya barranta da yanayin da yake ciki a zahiri a sace yake kallon Yakaka , yaƙi matsawa daga wajen kamar wanda aka dasa shi banda kokawa babu abunda yake da sofiya . Muryar Amnee ce ta dawo da shi cikin hankalin sa , inda take cewa , " ka jaa ta ku bar nan wajen nace bana son hauka da rashin kunya kana jina ko ? Da ƙarfi ya murɗa hannun sofiya , muryarsa cike da gargaɗi yace " ki nutsu Sofiya meye kike ne haka ? Ki zo mu tafi . Ta tsakanin Mata da yaran da suke tsaye carko-carko suka wuce yana riƙe da tsintsiyar hannun ta Sun zo kusa da sashin sa ta warce hannun ta da ƙarfi , muryar ta tana rawar kuka tace " Ka daina jana Hamza , ina wai za ka kaini ? so nake kawai ka faɗa min gaskiya , dan ni har yanzu ban yadda da abunda yake shirin faruwa ba . Matsowa yayi daf da ita yana satar kallon tsirarun mutanen da suke sabgogin su a harabar gidan yace " Sofiya kiyi haƙuri dan Allah muje ki nutsu na miki bayani.. Da ƙarin ƙarfin kukan da ta take yi tace " Bayani ? Bayanin me za ka min ? Doctor meye bana yi maka a zaman mu na aure da za ka min kishiya da wannan ƙazamar kuchakar Yarinyar ? Kuma ma wai har ka ɓoye min Doctor ka ƙi sanar da ni tun wuri da na yiwa tufka hanci . Kwantar da murya yayi yace " Sofiya wallahi ba ni nace zan aure ta ba Baa da Amnee ne suka haɗa lamarin nan , ki bari zan miki bayani sosai idan mun zauna, yanzu ki bar kukan da kike muje cikin ɗakina ki wanke fuskar ki , kin ga magariba ta gabato bana so na rasa jam'i , Juyawa tayi maimakon ta ɗau hanyar cikin gidan sai ta kama hanyar sashin Prof , a tsorace ya sha gaban ta wannan karon fuskar sa babu alamun wasa yace " Ina za ki ? Ita ma da wata irin faffaɗar murya tace " wajen sa zan je naji dalilin da zai sa ya mun haka , sannan kuma na roƙe shi dan Allah ya warware wannan mummunan ƙullin da yake son yiwa rayuwata , Muryar sa a dake da bayyanuwar ɓacin rai yace " Sofiya ki nutsu ki shiga hankalin ki , iyayena fa ba abun wasan ki bane , naga duk irin haukar da kika yi a gaban Amnee dan na miki uzuri dalilin cewa ke ma an miki kuskure ba hakan ne zai sa ki dunga yin duk abunda kika ga dama ba akan su , ki nutsu nan gaba zan iya ɗaukar mummunan mataki akan ki muddin kika nemi cin zarafin iyayena , Daga haka ya wuce ya bar ta a wajen , wajen famfon dake zubar ruwa ya nufa yana daura alwala , Da saurin da ya wuce ƙima Sofiya ta tasamma ƙofar gidan ta fita tamkar zata kifa , Zuciyar sa babu daɗi ya bita da kallo , wannan tashin hankalin yake gudu daga gareta yasa tun farko ya kasa sanar da ita , sam shi ba mutum bane mai ƙaunar hayaniya . Yana kammala Alwala ya shiga motar sa ya tayar aka buɗe masa ƙofa , yana fita kafin ya dai-daita kan motar a bisa titi ya hango motocin su Doctor Suleiman tare da na wasu abokan sa su huɗu , motoci biyar kenan , a sarari yayi tsaki kafin yace " wannan kuma Uban 'yan didimar sai da ya min gayyar da na ce bana so . Hannu kawai ya ɗaga musu tare da matsa ham , ya bi bayan sofiya wacce ya hango har ta kusa titi . Da kyar ta yadda ta shiga motar ya miƙa ta gidan su , sai dai ko ficewa a layin gidan nasu bai yi ba ita ma ta sake fitowa a cikin motar Momy kori da gudun gaske ta ɗau hanyar gidan gogaggen Malamin ta da ta yadda da shi ɗari cikin ɗari aikin sa na ci , aifa zama bai gan ta ba . Matar mutum bata zama ta wanin sa , washegari da misalin ƙarfe goma na safe taron jama'ar da suka cika suka tumbatsa suka shaida ɗaurin auren Hamza Mustapha Dilmari tare da Amina Muhammad Kalama . Bayan ɗaurin Aure walima ta biyo baya , abokan Doctor Hamza da suka tasamma su ishirin sun sanya shi a tsakiya gami da sauran dangi , bayan fara'a babu abunda yake kamar ba shi bane ya sha ɓacin-rai da jin labarin auren , Shi da kansa bai san takamaimai me yake bashi nishaɗi ba illa yasan wani ɗan tsiron farin-ciki ne daga can saƙon zuciyar sa da ya zata ya mutu tun-tuni yake sabunta kan sa a yau . Ɗan gefe guda Suleiman ya jaa shi bayan ya gama tsokanar sa yadda ransa ke so a ƙarshe yace masa ya kamata Amarya ta fito su gaisa saboda su anjima kaɗan zasu juya . Baya so ko kaɗan Suleiman ya fahimci akwai wani abu marar daɗi a tsakanin sa da ita saboda ko babu kome ita a yanzu wata ɓangare ce ta rayuwar sa ba zai so ya zubda mata da ƙima a wajen wasu nasa ba dan haka yace ," Abokina mu je daga sashi na a ƙira ta ta gaishe ka kai kaɗai amma sauran sa haɗu watarana kawai . " Ayi haka kuwa abokina ? Doctor Suleiman yace da ɗan shakku , hannun sa Doctor Hamza ya jaa tare da cewa "ai anyi ma , suka fara tafiya zuwa sashin sa yana ƙiran Amnee a waya , bayan ta ɗaga yake sanar da ita buƙatar sa na son a turo Yakaka sashin sa zasu gaisa ita da Suleiman . Cike da murnar da tunda aka ɗaura auren lafiya yake mamaye ta , Amnee ta miƙe daga bakin gadon ta da take suke zaune ita da wasu ƴan'uwanta suna tattaunawa ta nufi ɗakin da ta bari a ɗazu Hajje Nadiya tana shirya Amaren a ciki , Tana tura ƙofar idanun ta suka yi farin gani da kyakkyawar farar fuskar ta da yau hasken ta ya ninku har wani sheƙi take , tana ɗaukar idanu iyakar kyau Yakaka tayi sa cikin farar Lafayar da aka naɗa mata mai adon ƙananun flowers baby pink da ash color akan sissilkan yadin da aka mata siririyar doguwar riga da shima launin baby pink , kan ta an naɗa mata ɗaurin ɗankwali simple an soke mata shi a gashin ta . Rungume ta Amnee tayi ta sumbaci goshin ta kafin ta kamo hannuwanta da suka sha ƙunshi irin zanen ƙunshin mutan chadi jazur da su sun yi gwanin sha'awa , da manyan awarwarayen zinaren da Amnee ce ta bata su , suka daɗa fiddo martaba da kyaun hannunwan nata . " da hannu ta yafito Falmata wacce take tsaye daga bakin window da alama akwai abunda yake taɓa ran ta a dai-dai lokacin , taƙi yadda a mata makeup sai yar hoda da man baki masu kyau aka shafa mata a cewar ta idanun ta basu cika lafiya ba bata son makeup , ita ma shirye take cikin wani pink ɗin leshi da aka mata ɗinkin Buba da zane tayi kyau fes da ita an mata ɗaurin ɗankwalin da ya fiddo zagayayyar cikakkiyar fuskar ta da ta sake yin tuɓus-tuɓus tana sheƙi sakamakon gyaran Hajje Nadiya da fatar ta ta karɓa . Haɗa hannuwan su waje ɗaya tayi , tana cewa Falmata ," ki je ki raka Yayar ki sashin Yayan ku Babba zata gaisa da baƙi , idan sun gaisa ki tabbatar kin dawo min da ita hannu na yadda na ɗanka miki ita kin san yau ita tafi lu'ulu'a daraja . Ƴar kyakkyawar dariya Falmata tayi kafin tace " an gama Amnee watau yau ni ce ƴar jagora ba ni za'a jagoran ta ba kai Alhamdulillahi Allah mun gode maka da ka nuna mana wannan ranar, Amnee tana dariya ta roko su har ƙofar sashin ta ko'ina suka gifta ana ga Amarya ga Amarya ana bin ta da kallon sha'awa har da masu yi mata hoto , Falmata ita ta fara yin sallama a ƙofar falon , da aka musu iznin shiga ma sai da ta kai kusan minti guda a ciki kafin Yakaka ta saɓile takalman ta ta sanya ƙafafun ta ciki kan ta a ƙasa ta samu gefe zata zauna daga ƙasa , da sauri Falmata ta riƙo ta dai-dai lokacin da Doctor Suleiman ma yake cewa " Kai kai Amarya ya za ki zauna a ƙasa ? Tashi-tashi ƙanwata yau ai ranar ku ce kamata yayi ma a dunga miki yawo da kujera ta musamman dan zaman ki kin san yau ke da sarauniyar England matsayin ku kai-da-kai yake . A hankali ta ɗago kanta bayan ta zauna akan kujerar da Falmata take kai suna gaisawa da Doctor Hamza jin muryar sa raɗau tayi mata kama da na wanda ta sani , shima Doctor Suleiman yana ƴar dariyar tsokanar ta da yake sauran Kalaman bakin sa suka maƙale masa a maƙogoro ganin fuskar ta ɗauke da kwalliya da sheƙin Amarci bai hana shi ya gane ta ba duk kuwa da cewa ganin sa da fuskar tata sau biyu ne rak , amma ta riga ta zanu a zuciyar sa mafarkin ta a yanayi ya irin haka a gaban sa abune da ya jima yana yi , Sai dai a wannan karon zahiri ita ce a bayyane a gaban sa amma ba a matsayin ta sa ba da kullum yake hari , a matsayin matar aminsa na ƙud da ƙuɗ take , cike da ruɗanin da ya gagara ɓoyewa bayan ta ɗauke ido daga kan sa da sauri , yace " Abokina daman wannan ce Amaryar ta ka ? Daga Yakaka , Youssouf har falmata sai da zuciyoyin su suka sauya bugu da mabanbanta tunaninnika da ya musu dirar mikiya , Ɓangaren Doctor Hamza a take ɓakin-cikin sa ya nemi dawowa sabo abunda yake gudu kenan tun farin farko da kuma ya sashi tsanar ta , cuɗanya da tayi ta yi da mazaje . Da sautin da shima bai ɓoye ɓacin-ran sa ba a daƙile yace " eh ita ce , ki gaishe shi mana ku koma ciki . Muryar Yakaka na maƙyar-ƙyartar da ta ƙarawa Doctor Hamza tabbacin rashin gaskiyar ta ta gaishe da Doctor Suleiman da gumi yake tsattsafowa a goshi , yana share gumin ya amsa da " lafiya lau Aminatu , nayi muku murna kin ji Allah ya sanya Alheri . A ɗan kaikaice Doctor Hamza yake kallon sa lokacin da Yakaka da Falmata wacce jikinta yayi sanyi laƙwas da yanayin da ta gani a tare da su biyun suka fice daga falon . Kafin Doctor Hamza yayi wani yunƙuri Doctor Suleiman da ya miƙe tsaye cikin wani irin yanayin da yake bayyana alhinin da zuciyar sa ke ciki yace " Hamza ka min shigar sauri , why ? Amina da nake baka labari ita ce wannan Abokina ita ka Aura . Da sauri Doctor Hamza shima ya miƙe , kafin yace kome Doctor Suleiman ya sake katse shi cikin yanayin da yafi na ɗazu rauni , ya cigaba da cewa , " Na taya ka murna Abokina babu shakka Allah ya arzuta ka da kamilar Mace mai nagartattun halaye , ina taya ka murna sosai ina kuma yi muku addu'ar samun ɗorewar zaman lafiya babu shakka matar mutum daga gare shi take ... Katse shi Doctor Hamza yayi a mamakance yake cewa ," kana nufin wannan Aminar ita ce Amina , Amina da kake bani labarin ta ? " ƙwarai da gaske ita ce . Shiru su biyun suka yi baƙon yanayin da ya ziyarce su yana samun damar mamayar tunanin su , muryar Doctor hamza ta sake ratso wajen da yake cewa " Abokina Dan Allah ka bani labarin haɗuwar ku da duk wani abunda ka sani game da Amina . Bayan komawar su Yakaka cikin gida gaba ɗaya sai ta rasa sukuni sarai ta gane ko wanene abokin Yaya dakta , shine mutumin da ya dunga bibiyar ta da sunan soyayya tsawon shekaru wanda har Malama Maryam da Lubna sun san shi , sai yau ta tuno rana ta farko da ta fara ganin shi a duniya ranar da suka fara haɗuwa da shi da kan sa Doctor Hamza tare ta fara ganin su , shine wannan abokin nasa da ya ji tausayin su a lokacin da Doctor Hamza yake hora su kan fitsarin da Falmata ta yi masa a office har ma ya basu kuɗi yace su sayi hijabi su suturta jikin su . Sai yau ta gane shi gaba ɗaya , amma yanayin da ta hango a fuskar Doctor hamza kafin barin su falon bayan Suleiman ya nuna ya san ta ya bata tsoro , sanin da tayi daman ita a wajen sa abar tuhuma da zargi ce , tsoronta ya ninku lokacin da tayi hasashen kar Suleiman ya sake dasa zarginta a zuciyar Doctor Hamza . An cigaba da shagalin biki zuwa Yamma aka fara shirye-shiryen tafiya Dinner da dangin Mijin Rahima ne suka shirya saboda su nan Baa baya son ire-iren bidi'o'in baya yarda a kama waje a tafi biki kome za'a yi a harabar faffaɗan gidan ake yi , sai dai fa idan dangin miji ne suka shirya abunsu ko kuwa bayan an miƙa amarya gidan ta ayi ta can . Shiri ake ta yi sosai saboda har Amnee da Khaalty Rahima ma zasu su a karon farko saboda ta roƙi Baa yau ɗaya tal ya bari su tafi tare har da Yakaka da Falmata tunda shi yaƙi yadda a shirya ayi daga Aljihun sa . Albarkacin farin-cikin da yake ji na wannan ranar bai jaa gardama sosai ba yace su je amma a kula a kuma dawo da wuri . Ana gaf da tafiyar bayan isha'i Doctor Hamza ya shigo gidan da tunda ya fita raka abokansa bai dawo ba ya zarce gidan su sofiya wacce tunda aka ɗaura auren take ƙiran sa a waya daga ya ɗaga sai ta fashe da kuka tana ihu tare da cewa sai ta kashe Yakaka , Tun abun na ba shi dariya har ya fara damuwa sosai tausayin ta ya tsirga masa , shi shaida ne akan irin son da take yi masa yana tsoron kar wani abu ya samu ƴar mutane ta dalilin haka dan haka da yayiwa su Suleiman rakiya suka rabu cikin raha da barkwanci sai ya kama hanyar gidan su Sofi Kacha-kacha ya tarar da ita tayi manƙas cikin ƙwayoyin da ta dunga afawa , tun lokacin da labarin ɗaurin auren ya zo ma bayan a jiya sai da ta bi malamai kusan biyar akan lamarin duk kuma suka tabbatar mata kan cewa za'a yi aikin da zai sa a fasa auren a daren kafin gari ya waye , sai dai ga shi babu wanda aikin sa ya ci sai asarar kuɗi da ta tafka . Tun kuma a jiyan ta dunga ƙiran layin Samy baby amma bata samun ta , damuwar ta ta ninku ba adadi . abunda ya mummunan kaɗa masa ƴan hanji bai taɓa sanin Sofin sa na shan kayan maye ba , ashe duk ihun da take masa a waya bata cikin hayyacin ta ? Kwayoyi ta fara sha a sanadin ƙarin auren da yayi ? Ƙwalla ne suka tarar masa a ido yana jin takaicin uwa irin Hajja Kori da baza ta iya tanƙwara ƴar ta ba , tayi ko ta bari , da ya shigo gidan ma bai ganta ba ko tana ina ? oho Haka da kyar ya sha kokuwa da ita tana doddoke shi tana zagin Yakaka wasu lokutan har da Amnee da Baa , haka dai ya daure ya sa tayi wanka ya taya ta shirya yana yi yana rarrashin ta , ya rubuta Allurar da yake son yayi mata ya bawa maigadi ya sayo ya kawo ya danna mata , bayan ya haɗa mata tea ta sha kaɗan tayi bacci . A gajiye liƙis ya baro gidan , zuciyar sa cike da tunanin maganganun da Suleiman ya faɗa masa game da Yakaka yana zakwaɗin samun tabbacin sahihancin su . Bayan ya zauna akan kujerar falon sa a kasalance ya ɗau wayarsa tare da ƙiran layin Amnee Khaalty Rahima ce ta ɗaga ƙiran saboda Amnee ta shiga wanka , bayan sun gaisa yace da ita " yunwa yake ji dan Allah a samar masa da abinci ," Abincin sa na musamman da daman yake kitchin ɗin sama a ajiye can ta hau ta ɗauko masa tana saukowa suka yi kichiɓus da Yakaka wacce ta fito daga ɗakin su zata shiga ɗakin Amnee , Da sauri ta ƙarasa ta karɓi tiren hannun Mamar su tana mata sannu , cike da jin daɗi Khaalty Rahima ta amsa , kafin ta ɗora da cewa yauwa Yakaka ga abincin yayan ku ɗauki ki kai masa , banda ma shirmen ki kina nan kina ta kai kawo mijinki yana can zaune da yunwa ,ki sauya wannan ɗabi'ar tun wuri dan naga alamar duk jaan kunne da nasihar da ake miki ba ganewa kike ba ki sa hijabin ki ki kai masa . Saƙare Yakaka tayi tana kallon Mamar su , so take ko yaya ta samu ƙafar zillewa amma babu dama , ji tayi ta cigaba da cewa " ki kai ki dawo yanzu idan kuma ba haka ba a tafi a barki na ga ma ko gama shirin baki yi ba . Ɗaki Yakaka ta koma ta saka dogon hijabin ta akan doguwar rigar da take jikin ta mai guntun hannu da fitowar ta kenan a wanka ta zira ta a jikin ta ta fito ɗaukar kayan ta a ɗakin Amnee shine wannan tsautsayin ya gifta mata , " ah tsautsayi mana haɗuwar ta da Yaya dakta ai ita tsautsayi ne a wajen ta mutumin da babu wanda ya tsana ya ita ? Cikin takun rashin kuzari ta nufi sashin nasa riƙe da tiren da aka jera abincin akai , tana taɓa ƙofar ɗakin da nufin ƙwanƙwasa ta ƙofar tayi baya a buɗe take , Sai ta shiga a hankali siɗak-siɗak ta ajiye abincin aka ƙasa , zuciyar ta ta ɗan yi sanyi ganin baya falon , tana ɗaga ƙafa da zummar barin wajen ta tsinkayi muryar sa a ɓakin ƙofar ɗakin sa , " Yace " ina ruwa ? Dan Allah a kawo min ruwa , ruwan cikin Fridge na ya ƙare . Bata juyo ba tace "akwai ruwa a ɗaya cooler ɗin , Jin muryar ta ya sa shi ɗago kai da sauri daga goge kan sa da yake yi da towel fitowar sa kenan daga wanka jikin sa sanye da jallabiya , Da sauri ya dakatar da Yakaka wacce ta ɗaga sawu tana son ɓacewa daga falon , " zo ki zuba min , yace da sauti marar ƙarfi , kanta a ƙasa ta juyo ta ɗau daya daga cikin plate biyu da suke kan faranti ta fara ƙoƙarin zuba aɓincin , Da sauri ya dakatar da ita , " kar ki zuba , chak ta tsaya zuciyar ta na harbawa , jinsa tayi daf da ita ya kai hannu a hankali ya zare plate ɗin daga hannun ta , banɗakin sa ya koma ya ɗaureye plate ɗin tare da chokula biyu , ya dawo ya miƙa mata, ta miƙa hannu biyu ta karɓa , da ido ya bi hannun ta da ya sha ƙunshi . " Ya isa yace , lokacin da ya ga tana ƙoƙarin cika masa Plate har ya tunbatsa , kan ta a ƙasa ta miƙa masa , ya karɓa yana kallon fuskar ta , kafin tayi wani yunƙuri yace mata " ki dakata na gama ci kar ki tafi , A ɗarare ta zauna daga gefe a ƙasa ta sunkui da kai , yana daf da kammala cin abincin Amnee ta ƙira wayar sa , yayi hanzarin ɗauka ," tambayar sa tayi ina Yakaka ? Ka turo ta yanzu ta gama shiri kowa ya shirya ita ake jira har wasu sun tafi , Cike da nutsuwa da kwantar da kai yace " Amnee wani wajen za'a tafi ne ? A gaggauce ta amsa masa da " eh wajen Dinner ɗin Rahima zamu tafi tare baki ɗaya , ta ƙarasa da cewa " ka turo ta yanzu kaji ko ," "Amnee , amm Amma kuma zuwa dinner har da ita ? Da dai ita ta zauna a gida Amnee ba wani amfanin fitar ta a daren nan tun... Muryar ta a ɗan sama Amnee tace "kai kar ka min tsarin wofi ka turo ta mu tafi yau dai ɗaya tal taje , tunda ita ba'a shirya mata nata bikin ba . Zai sake yin magana ta kashe wayar tana cigaba da yiwa Khaalty Rahima mitar meyasa ta aiki Yakaka sashin Doctor Hamza ? Ga shi zai kawo mata wani iyayi irin na shi . Murmushi kawai Amnee tayi tana mamakin rigimar Amnee marar tushe , mutum da matar sa a hana ta yi masa hidima ? Hankalin sa kwance ya ƙarasa cin abincin sa , cikin ran sa neman hanyar da zai hana fitar Yakaka zuwa wajen wani taron can daban yake , a haƙiƙanin gaskiya baya son ta fita da auren sa cikin wasu ƙattin wofi ,su gama ƙare mata kallo , wanda aka kalla a da ma ya isa , duk da cewa dai wasu maganganun da Suleiman ya faɗa masa sun saɓa sosai da zaton da shi yake mata . Yakaka ta durkusa ta tattara wajen ta haɗe kome yadda ta zo da shi , a hankali ta miƙe zata fita , cikin rashin sanin ta ta taka bakin dogon Hijabinta , saboda sauri da take ta bar inda yake , bata ƙarasa miƙewa ba Hijabin ya taɗile ta tayi ƙasa baki ɗaya farantin hannun ta ya bigi ɗan teburin gabanta , miyar da bata rufe sosai ba ta buɗu cooler ɗin yayi ɗan tsallen da yasa miyar tankwaɓewa ta fallatsuwa har cikin idon ta kafin ta kwaranye mata baki ɗaya a jikinta . Ɗumin miyar tare da zafin attaruhun ciki da ya shiga mata ido yasa bata san lokacin da ta saki wani ɗan ƙaramin ihu ba . A ruɗe Doctor Hamza ya miƙe yana jera mata sannu , amma azabar da take ji a idanun ta yaƙi barin ta nutsuwa bare ta ji me yake cewa , ihu ta shiga yi tana cewa " wayyo idona , Da sauri ya riƙo ta ya kama hannuwanta duk biyu zuwa cikin ɗakin sa ya zarce da ita cikin bathroom , gefen Bath ya zaunar da ita , duk a ruɗe yake da ihun da take yi ya kunna fanfo lokacin da ya ɗauki handle ɗin shower yana tara ruwa a hannun sa , ruwan ya kai ya wanke mata fuskar da shi ya sake cika hannun sa ya wanke mata , Yayi hakan sau kusan huɗu amma bata daina kukan da take yi ba , sai kawai ya juya shower ɗin ya shiga fesa mata ruwan a fuska yana haɗawa da wanke mata idon sosai da ma fuskar ta baki ɗaya , Hannun sa ta ture lokacin da ta ji raɗaɗin ya ragu sosai , ta fara ƙoƙarin buɗe ido , " ya ya ? Ya fita ? Ya tambaye ta cikin taushin murya bayan ya ɗan yi durƙuso a gaban ta yana leƙen idon nata so yake ya ga ta buɗe su , Tana buɗe idon ta runtse su da ƙarfi jin har yanzu da sauran raɗaɗi , bata ankara ba ta ji ya ɗago haɓar ta ya matso da fuskar sa daf ta ta , hannu ya sa ya tallafe ƙeyar ta ya fara hure mata idon a hankali Sassanyar iskar bakin sa tayi tasiri sosai wajen rage mata raɗaɗi , ta kuma taimaka wajen dawo mata da nutsuwar ta , har ma ta fahimci irin kusancin da yake tsakanin su , zuciyar ta ta ji ta buga ɗas! Da hanzari ta buɗe idanun ta da suka ɗan rine suka kunbura kaɗan , suka yi musayan kallo da ita da shi , nitsar da idanun sa yayi cikin nata yana yawo da ƙwarar idanun sa a tsakanin nata , ji yake tamkar wata dama yau ya samu na gano tare da tsamo abunda yake hangowa a cikin ƙwarar idanun ta da yake kashe masa jiki a duk lokacin da ya fiye kallon su , Tsintar kan ta tayi da gaza janye idanun ta , fuskar sa dake daf da ta ta take ƙarewa kallo , sajen da ya bari da yake ta sheƙi a hasken lantarki ya ɗau hankalin ta , kamar ta kai hannu ta taɓa , Ganin yadda ta shagaltu da kallon fuskar sa yasa shi hure mata ido , da sauri ta sake rufe idanun nata , Kamar an farkar da ita sai ta miƙe tsaye da sauri , ta ɗan matsa daga kusan shi sosai sai lokacin ta ankara da jiƙewar da kayan ta yayi sharkaf ,tundaga kan hijabin jikinta har rigar ta ta ciki . " shine ka jiƙa ni haka ? Yanzu ya zan yi ? Ta furta hakan muryar ta cike da shagwaɓar dake nuni da damuwar da zuciyar ta ke ciki , Miƙewar shima yayi ya ɗan wara hannu kafin ya nuna mata nasa jikin da yake jiƙe shima , yace " ku ji ta kamar ba ke kika ruɗani ni ba kika sa na jiƙa jikina , raguwa kawai kin sa yanzu dole na sauya kaya . Kewaye ta yayi ya fita kai tsaye wardrobe ya nufa ya zaro wata jallabiyar ya tuɓe ta jikin sa yana warware ɗayar Yakaka da ta matse ruwan jikin kayan ta ta murɗo ƙofar a hankali ta fito , Da fitowar ta da hango shi ba riga da komawar ta cikin banɗakin ta rufo ƙofar da ƙarfi duk cikin abunda yake ƙasa da minti guda ta yi su , Doctor Hamza da duk abunda tayi akan idanun sa , har A'uzubillah da tace kafin komawar ta cikin banɗakin duk ya ji ta , Ɗan wani guntun murmushi yayi lokacin da wani tunani ya gifta masa nan take , rigar da yayi niyyar sawa ya ajiye a gefen gadon , a nutse ya nufi ƙofar banɗakin , ba tare da ya taɓa ƙofar ba yace , " ki fito ki tafi kar a gaji da jiran ki . Daga ciki ta ce " to ka gama shiryawa ko ? Dan Allah kayi haƙuri ɗazun ban san kana shiryawa bane , Ɗan mitsitsin murmushi ya kuma yi yana cije leɓensa na ƙasa a taƙaice yace " eh na shirya ki fito . Kan ta a ƙasa ta fito , a ɗan sace ta ƙyallo sa ,ta gan shi yadda yake a ɗazu da sauri sake juyawa sai dai kafin tayi wani yunƙuri ya naɗo ta ta cikin jiƙaƙƙen Hijabin ta ya haɗa ta da jikin sa , A ruɗe Yakaka ta fara ƙoƙarin ƙwacewa , bakin ta ya gaza furta ko kalma guda , matsera kawai take nema , " Meye kike haka , kamar wacce bata saba ganin Maza a tuɓe ba ? Kar ki min kinibibin ku na mata . Doctor Hamza yace haka laɓɓansa ɗauke da murmushin da yafi kama da na mugunta , cikin zuciyar sa yana sake haƙaƙewa da abunda yayi niyya , ya juyo da ita da ƙarfi ya ɗago fuskar ta da idanun ta ke runtse , hasken da ya haske fuskar shi ya bashi damar ganin hawayen da suka jiƙa mata fuskar ta , Shagala yayi da kallon kowanne ɗigo na tudu da ƙwarmin da yake fuskar ta , kallo yake mata irin wanda bai taɓa yi mata irin sa ba , a idanun sa kome na fuskar ta tsararre ne da ya dace ƙwarai da muhallin da Ubangiji ya ajiye mata shi . Zuciyar sa take buɗuwa tare da tashin tsikar jikin sa, bai san lokacin da ya haɗe tazarar da bata wuce tudun yatsa guda da yake tsakanin fuskokin su ba , ya haɗe fuskokin su waje guda , tare da ratsa hannuwan sa ya kewaye ta da su sosai , Da wani irin yanayin da ya zarce yadda yake da nufin yi , ya shiga yin abubuwan da zuciyar sa ta raɗa masa da ya yi a matsayin gwada Yakaka ya ga ko kalaman Suleiman gaske ne Yakakar kamilallar mace ce , tsautsayi tare da kaddarar rayuwa ce suka faɗa mata ? Sai ga shi ya gaza tantance Yakaka yake son gwadawa ko kuwa martabar sa ta ɗa Namiji yake aunawa ? Domin kuwa a tsakanin lokacin jin sa yake kamar wannan ne lokaci na farko da gangar jikin sa ya fara raɓar na wata ɗiya Mace . Yakaka da ake yiwa gwaji ita ta yunƙura ba tare da tayi amfani da ƙarfin kirki ba , ta zare jikin ta daga na shi , bata tsaya ba kamar yadda bata yadda ta bari idanun su sun haɗu ba ta taka da gudun gaske ta fice daga ɗakin da sashin nasa ma baki ɗaya , Bata tsaya daga gudun da take yi ba sai da ta tabbatar ta bada tazara mai ɗan yawa daga sashin sa . Zama tayi akan wani ɗan tudu tana mayar da numfashi harabar wajen babu mutane alama dake nuna an riga an tafi Dinner an bar ta . Kalaman Doctor Hamza ta tuno ," me yake nufin da cewa ta saba ganin maza a tuɓe ? Kenan nufin sa ita wata ƙasurgumar karuwa ce da ta saba cuɗanya da Maza , shi yasa ya mata abunda ya yi mata yanzu . Hawayen ɓakin ciki ya zubo mata , tayaya zata yi rayuwa da mijin da yake zargin ta irin wannan mummunan zargin ? Da jaan ƙafa ta nufi cikin gida , kai tsaye ta zarce ɗakin su inda ta tarar da Falmata ita ɗaya ƙwal tana kwance lamo akan gado Bata ce mata ƙala ba kamar yadda ita ma Falmatan bata nuna alamun ta san da shigowar ta ba , ta cire jiƙaƙƙun kayan jikin ta sauya da wasu , a hankali ta zo bakin gadon ta zauna , ta ɗan dubi Falmata da jikinta yake bata ba bacci take ba ƙoƙarin haɗiye damuwar ta take lokacin da tace , " Falmata baki tafi wajen Dinner bane ? Ba tare da ta motsa ba muryar ta can ciki tace " Ban tafi ba Yakaka Amnee tace na zauna nima tunda ke ma Yaya Dakta ya hana ki tafiya , kuma ma bana jin daɗin jikina bayana ciwo yake min . Shiru su dukkanin su biyun suka sake yi , zuciyar kowaccen su na sake ƙuntata da damuwar dake cin ta a rai , can ta tsinkayi muryar Falmata tace , "Yakaka yau kwanan mu ishirin da ɗaya da dawowa daga Niger ko ? Ɗan waigowa Yakakar tayi ta dube ta , ba tare da ta bata amsa ba tausayin ta ta ji ya kama ta , babu shakka tasan damuwar Falmata ba zata wuce akan Youssouf ba da shima yake gwada nashi walaƙanci a zaton ta ta hanyar yin shaƙulatin ɓangaro da ƙanwar ta . Washegari duk baƙi na nesa suka fara watsewa ciki har da Malama maryam da duk wasu dangi na nesa suka yi tafiyar su bayan Amnee ta cika su da kayan biki fal . Zuwa yammaci gidan ya rage sai su isu 'ya'ya da dangin Amnee , lokacin ne kuma Baa ya aika aka ƙira masa Doctor Hamza , bayan sun gaisa nasiha ya shiga yi masa mai ratsa jiki tare da tarin tunasarwa akan nawin da ya ƙaru akan sa , da kuma wuyar da yin Adalci yake da shi wanda kuma dole ne ya tsayar da shi a tsakanin matansa muddin yana son dacewa da samun Rahamar Ubangiji . Bayan ya gama masa nasiha da hannu ya masa nuni da saitin akwatuna biyu da adadin su yake kai ɗaya kawai launi da sumfurin su ne ya shabanba , kowanne guda takwas , ya ɗora da cewa " Wannan lefen Matan ka ne ɗayar ka kaiwa Safiya da hannun ka , ɗayan kuma na Amina ne , kamar yadda muka yi da kai nan da ƙasa da watanni biyu nake so ka samarwa da matar ka wajen zama a kusa da kai , idan ma kuma wajen zaman ya samu a yau ko gobe ne ka dawo ka ɗauke ta ku tafi abun ku Allah ya bada zaman lafiya . Godiya Doctor Hamza ya dunga yi ƙaunar Mahaifinsa na daɗa ratsa shi tare da ƙarin ganin ƙima da darajar sa , har ya miƙe zai tafi Baa ya sake dakatar da shi wata ɓakar leda da take nannɗe ya miƙa masa "wannan kuma wasu kuɗaɗe ne da aka bani na baka a matsayin gudumawa , ka ƙara wajen kula da gida , Da sauri Doctor Hamza ya noƙe hannun sa ," Baa ka bar su ayi amfani da su anan , ni ina da kuɗin da zasu isa nayi kome da su Nagode Baa nagode . Da murmushi a fuskar sa yace" karɓi mana ai ni na baka . Ƙarfe biyun rana Doctor Hamza yayi Sallama da iyayen sa zai koma Abuja a yau ɗin saboda gobe yana da tarin aiyuka a office da bashi da damar ɗaukar musu uzirin jinkirta yin su . Dangin Amnee ma ya musu Sallama bayan ya bada kuɗaɗe masu yawa da yace ayi musu sayayyar duk abunda suke so kafin tafiyar su , sannan ya tsawaita godiyar sa a gare shi . Da Khaalty Rahima ma sallamar su ta musamman ce da suka keɓe suna yi ta inda ita ma ta ɗora masa 'yar nasihar ta a ƙarshe ta ba shi shawara kan ya lallashi Safiya sosai kar ya bari ƙarin auren da yayi ya ɓata zamantakewar su . Ƙannen sa mata ma duk Sallamar yayi da su har da Rahima amarya da ba'a riga an miƙa ta gidan mijin ta ba saboda iyayen sa ba 'yan nan bane 'yan ƙasar katsina ne , kuma a halin yanzu duk suma shirye-shiryen komawar su suke can ƙasar America inda suke rayuwar su a can , nan da ƙasa da sati biyu zasu tafi tare duk har da Rahima . Lokacin da ya gama Sallama da kowa da ya dace , ciki har da Falmata, sai ya shiga ɗan jefa ido waje-waje ya gagara tashi ya tafi , sai daɗa jaan hirar su yake shi da ƙannen sa . Hajja wacce ita ma tun a waje da ita ya fara cin karo tana tattara harabar gidan suka gaisa har ma ya mata sallamar tafiyar sa ta jero masa addu'o'in da yake jin daɗin irin su , Ita ce ta shiga tana ganin sa tace ," Babban likita har yanzu baka tafi ba ? Kai kuwa na ga baka saba tafiyar dare ba garin Abuja ai ba kusa ba , dan ma dai ku manya ne . " yanzu zan tafi Hajja , yace yana ƙoƙarin miƙewa , Hajja ta shige ɗakin ta tana cewa " Allah ya tsare hanya Babban likita . Tana shiga ɗakin tayi turus ganin Yakaka kwance akan katifar ta tana buga game da wayar Rahima , Salatin da Hajja ta ɗauka sai da ta dire shi da tafa hannuwa sannan ta ɗora da cewa " ni hauwa'u me zan ji me zan gani ? 'yar nan kan ki ɗaya ? Yakaka ta ɗago kai tana kallon Hajja , " me nayi Hajja ko dan na hau 'yar katifar ki ? to bari na tashi , ta ce tana miƙewa ta sauƙa daga katifar ,fatan ta shine Hajja tayi shiru kar a jiyo muryar ta a san tana nan . Hajja ta ɗora da cewa " tambayar ki nake kan ki ɗaya ? Yanzu ace Mijinki na can shirin ɗaukar doguwar hanya ke kina nan kina latse-latsen wofi ? Bawan Allah shi yasa mana ya gagara tafiya ashe ke ce baki masa abunda ya dace ba wanda zai ƙara masa kuzari da nishaɗin tafiya , tashi nace sakaryar mata , tashi ki fice min a ɗaki , ki fita ga mijinki can yana jiran ki kuyi sallama . Hafsa da zainab da duk abunda Hajja ke cewa daga ɗaki suna jin ta sarai saboda sama-sama take maganar sai suka haɗa ido kafin su duka ukun su kwashe da dariya , Falmata ma sai da ta ɗan dara , a ran ta tana aiyana wannan kaɗan ne daga halin Hajja , yadda aka san bata da wani aiki sai na faɗin yadda mace za ta farantawa miji Ho Hajja , ya dace a bawa Hajja shugabantar wata ƙungiya ta faɗakar da mata kan yadda ake tafiyar da Miji . Hafsa ita ta rage dariyar ganin yayan su na tsaye yana kallon su , ita ma sai ta ɗan ɗaga murya lokacin da take miƙewa tsaye tace , "Ƙanwata Amarya ki fito kuyi sallama big bro zai tafi idan kuma ma mu kike jin kunya , kun ga ku zo mu bar wajen tace da sauran 'yan uwan ta , nan take suka miƙe suka yi ɗaki suna ƴar dariya tare da sake yiwa yayan su fatan Allah kiyaye hanya , Doctor Hamza da yake tsaye hannun sa a zube cikin Aljihun rigar rigar jumfa jikin sa , ya ɗan gyaɗa musu kai da murmushi a fuskar sa , shi ɗaya ne ƙwal ya rage a falon . Ganin sa ya mayar kan ƙofar ɗakin Hajja lokacin da Yakaka ta buɗo ƙofar ta fito kan ta a ƙasa fuskar ta kadaran-kadahan , ɗan matsawa kaɗan tayi ta bayan kujerar falon ta ɗan durkusa , " ina yini yaya dakta , Bata jira ya amsa ba ta ƙara da cewa " Allah ya kiyaye hanya , Bata yarda ta dubi sashin da yake ba bare ta san cewa ya matso kusan ta sai da ta miƙe tana shirin wucewa ta shige ɗakin su da yake kusa da ita , sai kawai ta ji ya riƙo hannun ta , A hankali ya jawo ta ya kusan haɗe jikin su , hannuwan sa yasa ya kewaye kunkumin ta , yana kallon fuskar ta da taƙi yadda ta ɗago kai , muryar sa ƙasa-ƙasa yace " haka ake yin sallama ? Babu addu'a ? Baki ji Hajja tace ki min abunda zai bani kuzari bane ? Da sauri ta ɗago kai , signal ya mata da duk girar idanunsa biyu , yana 'yar dariya da fararen haƙoran sa da suke da kyau sosai akan fuskar sa mai rangwamen haske . Ɗauke kai Yakaka tayi gefe can cikin ranta tana mamakin meyasa ta hango kamar sauyin mu'amala a tare da shi daga jiya zuwa yau ? muryar ta cikin sanyin tace " ai nace Allah ya kiyaye hanya na yi addu'a , Hannun yasa ya sake juyo da fuskar ta saitin sa , ya zarce da sanya ɗan yatsan sa ya shafa saman idon ta , da yasa Yakaka ta lumshe idanun ta da sauri , " Ya idanun ki sun wuce ko ? Basu sake damun ki ba ko ? Ya tambaye ta da ragwan sauti , gyaɗa kan ta tayi tana ƙoƙarin kautar da fuskar ta , amma ya ƙi bata damar haka sai ma hannuwan sa duk biyu da yasa ya tallafi fuskar ta yana shafa kumatun ta masu taushi yace ," to ina saurarar ki ki min Duas kuma ki min abunda Hajja tace ki min , ko bakya so na samu kuzarin tuƙin ne ? Sallamar wata baƙuwa ya sa Yakaka ta fisge jikin ta da ƙarfi da daman baki ɗaya a takure take damar gudu take ta son samu , Sai dai bai bata damar gudun ba ya riƙe hannun ta lokacin da suke gaisawa da matar ya san ta ɗaya daga cikin mutanen Amnee ce , ta zauna akan kujera. " Ba za ki min Duas ɗin ? ba yace yana jaan hannun Yakaka su fice daga falon , babu yadda ta iya ta bi shi sai dai suna fitowa suka hango Amnee na tahowa daga sashin Baa , " Yaa Doctor Allah ya kiyaye hanya ya kai ka lafiya , ya kare ka , ta harhaɗo kalmomin cikin sauri tana ƙoƙarin kwace hannun ta daga cikin nasa , kafin ƙarasowar Amnee ya sake ta da sauri ta taka tana komawa ciki , da murmushi ya bi bayan ta da kallo wani irin nishaɗi ne mai daɗi yake huɗa shi . Ƙarfe uku ya ɗau hanyar Abuja tare da sofiya wacce ya biya gidan su ya ɗauke ta dole bayan ya mata jaan ido tare da barazanar barin ta ta cigaba da zama a gidan su na wasu kwanaki da take son yi dai-dai yake da rabuwar su baki ɗaya , jin haka ba shiri ta tattaro ƴan kayan ta ta bi shi, ba tare da ta kula Momy kori sun yi wata sallamar kirki ba saboda haushin ta da momy kori take ji . ASSALAM ALAIKUM MASU KARATU DA FATAN KUNA LAFIYA ? INA GODIYA DA YADDA DAI HAR KULLUM KUKE HAƘURI DA NI . INSHA ALLAH SHAFI NA GABA SHINE ƘARSHEN LITTAFIN MHR DA ZAI BIYO BAYA NAN BA DA JIMAWA BA. NAGODE [1/17, 9:40 PM] +234 706 503 6187: MAFARI ( Hargitsin Rayuwa) Umm'muaz 49 MARADI-NIGER Kwanakin da suka biyo bayan bayyanuwar mummunan aikin da Gimbiya maimounatou ta aikatawa Biyamuradi Youssouf , tare da sa hannun Mammadou da Hajiya Mama , Masarautar maraɗi ta kasance cikin alhini mai tarin yawa , kusan kullum aka yi zaman fada da Waziri ne ke jagoranta ba'a da wani batu da ya wuce na sake tattaunawa kan wannan mummunan lamari haɗi da yiwa Biyamuradi Addu'ar samun lafiya tare da fatan dawowar Maimartaba . Da har yau da suke cika kwanaki ishirin da ɗaya basu baro india ba , Amma ana saka ran dawowar tasu a yau ko gobe saboda saƙon yiwuwar dawowar tasu ya iso musu . Akwai labari daga majiya mai tushe cewar gimbiya Siyama tare da ƙanin Biyamuradi Youssouf , 'Bilal wanda shine mai binsa a haihuwa sun fara shirin tafiya India domin cigaba da jinyar sa da har kawo yau babu wanda yasan takamaimai a halin da lafiyar Youssouf ɗin ke ciki . Ta ɓangaren Hajiya Mama kuwa duk yadda ta kai ga sanyawa idanun ta toka ta mustsiƙe ta cigaba da yin harkokin ta yadda ta saba , amma ta gagara domin yadda labarin sa hannunta da na ɗan ta wajen yunƙurin kisan da Matar Biyamuradi tayi masa , ya bazu ba a bakin bayu da hadiman cikin masarautar Maradi kaɗai ba har jama'ar gari da na wasu jahohin labari ya kai musu . Ake kuma kucin-cina labarin tare da sake liƙa masa baƙaƙen sassa ana sake munana sa ba ƙaramin tasiri hakan yayi wajen kassara mata duk wani karsashi haɗi da ɗagawar da take tinƙaho da shi na kasancewar ta matar Sarki . Dan haka gaba ɗaya sai take neman zama mujiya , tsarguwa take da irin kallon da bayun gidan suke mata , gefe guda ga dumuwowi birjik da suka mata ƙawanya , wanda bata saba shiga makamantan su ba , mafi girman su halin da ɗan ta tilo namiji yake ciki wanda yake tamkar ga ƙoshi ga kwana yunwa a wajen ta , domin kuwa tasan muddin Youssouf ya rasa ransa, cikin hakan akwai yiwuwar shima Mammadou ayi masa huƙunci mai tsauri da ka iya kawo ƙarshen shima tasa rayuwar . Ga Maimartaba da bata san matsayin ta takamaimai a wajen sa ba , bayan tonon sililin da Maimounatou tayi mata a gaban sa , gefe guda kuma ga Mairamar sarki da take autar ta sannan mafi soyuwa a wajenta cikin 'ya'ya da tun bayan faruwar wannan lamarin da ta samu labarin kome bayan kuka bata wani taɓuka abun kirki , Rufe kanta take a ɗakin ta da yake sashin uwar-riƙon ta , ( Hajiya Umma ) ta ci kuka ,domin lamarin ya mata tsauri wajen ɗauka duka biyu a lokaci guda , dan kuwa bayan kasantuwar Youssouf yayan ta mafi kusanci da yawan ƙauna a tsakanin su fiye da duk sauran 'yan uwan ta , ta shaƙu da shi tunda ta buɗi ido ta ga kanta riƙe a hannuwan sa , shiga hatsarin rasa shi ba abune mai sauƙi a wajen ta ba . Damuwar ta tana sake hauhawa da hango rugujewar zancen auren ta , tare da ma guntilewar alaƙar su ita da masoyinta da suka ɗibi tsawon shekaru uku suna soyayya wanda yake yaya ne ga gimbiya Maimounatou , uwa ɗaya uba ɗaya gaf ma ake da yanke ranar auren su cikin watannin gaba kaɗan a sha biki , sai ga shi wannan mummunan lamarin ya shata layi a tsakanin su , domin kuwa ko ba'a sanar da ita ba ta san makomar soyayyar su ita da Khaalifa , sannan tun kafin a hana ta ita ya kamata ta fara zare soyayyar sa daga ran ta , bayan abunda ƙanwar sa ta aikata ga Biyamuradi ai babu wani sauran alaƙa mai girma da zai sake shiga tsakanin masarautun nasu biyu . Ba tun yau ba ta riga ta san wasu daga cikin munanan halayen Mahaifiyar su da ita koyaushe huɗubar ta tare da yunƙurin ta bai wuce na ganin ta raba kyakkyawar alaƙar da ke tsakanin ta da uwar-goyon ta tare da sauran ƴan uwan ta da suka haɗa uba ɗaya ba , da ita kuma ko kusa bata ganin aibun su , sannan duk wasu laifuka nasu da hajiya Mama ke faɗin sun aikata ko suna kan aikatawa , ita bata kai ga kama su da ko guda ba dan haka koyaushe take biris da huɗubar ta , tare da toshe kunnuwan ta , ƙaunar ƴan uwanta a jinin ta yake tana ƙaunar su kwatankwacin ƙauna tare da zallar kulawa da su ma suke nuna mata a matsayin ta na ƙaramar ƙanwar su , ga hajiya Umma kuwa ba zata ce kome ba da ya wuce fatan alheri tare da godiya ,riƙo ta mata na haƙiƙa ba irin riƙon ƴar kishiya ba , dan haka take jinta basu da wata maraba da Hajiya Mama , sau dayawa ma tafi kusanci da Hajiya Umma akan ita Hajiya Mama ,( goyo guba ) Amma ace sanadin son zuciya irin na Hajiya Mama duk ta rusa mata farin-cikin ta a lokaci guda ? Gani take kamar Hajiya Umma da sauran ƴan uwan ta duk zasu tsane ta akan laifin Mahaifiyar ta da ɗan uwanta , a tsakanin hakan take yawaita tambayar kanta anya kuwa tayi sa'ar uwa ??? An cigaba da tsare Gimbiya Maimounatou tare da Mammadou a Niamey , saboda rashin sanin halin da Youssoufa ke ciki ya hana a tura su ga kotu , kawo yanzu kuwa Mammadou iyakar nadama ya yita , ko abincin da ake ɗan kawo masa , baya iya ci duk ya lalace yayi duhu , bai taɓa zaton akwai wani lokaci da zai zo yayi danasanin zazzafar ƙiyayyar da yake yiwa ɗan uwan sa ba irin wannan lokacin da ya sarƙe cikin sharrin Gimbiya Maimounatou da ta tsaya kai da fata kan shi ya kawo mata gubar da ta ciyar da Youssouf da a zahiri ba gaskiya bane ba shi ya kawo mata ba ,ba shi kuma da wata masaniya akan haƙiƙanin me ya faru ga Youssouf a wannan daren , iyakar abunda ya sani shine yaje gidan Youssouf mintoci kaɗan bayan ƙiran sa da tayi saboda kusancin da yake tsakanin gidajen nasu biyu da wuri ya isa , ƙarƙashin jagorancin gnala da ta tare shi tun a babbar ƙofar gidan ya cimma har falon da Youssouf ke yashe a ƙasa cikin halin fitar hayyaci , a lokacin shi da kansa ya shiga ruɗani ganin halin da ɗan uwansa ke ciki , a ɗimauce ya shiga tambayar gimbiya Maimounatou " Ya mutu ne ? Da gaske Youssoufa ya cimma kushewa tai ? Bai gama tantance da abunda ke faruwa ba lokacin da suka tsinkayo jiniyar 'yan sanda , Kallon-kallo aka yi tsakanin su ukun , da ruɗani ya bayyana a fuskokin su sannan da wani irin sauti Gimbiya Maimounatou tace , " Mammadou ka shigo da ha'inci cikin lamarin mu amma kayi kuskure ka kuma yi shuka a idanun maƙwarwa , muddin kuwa baka yi wani yunƙuri ba tarkon da kayi na iy afkawa har da kai da makusantan ka , Cikin ruɗewa yace , "ki bar surutan banza ki faɗi wanne tanadi kika yi kafin ki aikata wannan aikin domin nayi gaugawar shafe girman laifin ki kafin lokaci ya ƙure miki , ko kin manta Yarima ɗiyan sarki kin ka kashe ? Kafin yin wani yunƙuri mai girma jami'an tsaron da bai kai ga tantance kakin soji ne a jikin su ko kuwa na 'yan sanda ba , suka dunga tururuwar shigowa falon kafin ya farga sun cika falon , bai shaida fuskar ko ɗayan su ba , sai fa Tafeeda da shi kuma tun shigowar sa ya rufu ga Youssoufa bakin sa ɗauke da sallalami gami da addu'o'i . Hanjin cikin sa ya kaɗa lokacin da ya lura jami'an tsaron wajen riƙe suke da bindigogin su da suke ɗane a saitin su shi da gimbiya Maimounatou , tsoro mai girma ya ziyarce shi lokacin da ya farga da tsaka mai wuyar da yake ciki , da dukkanin alamun da suka bayyana ya taka sawun ɓarawo . masaniyar sa ɗaya shine yasan gimbiya maimounatou tana da mummunar manufar kashe Youssouf tun shekarun baya da ta taɓa furta musu hakan shi da Hajiya Mama lokacin da suka yi wata ganawa ta sirri da su da ita wanda a lokacin suka haɗa hannu wajen ganin sun kai Youssouf ɗin ƙasa da shi da Hajiya Mama ba burin su kashe shi ba , ( kashe shi abune wanda ba sa hangowa kansu hanya mai ɓillewa ta nan ) kwaɗayin su tozarta shi suke irin tozartuwar da zata kai shi ga rasa damar sa ta hawa ƙaragar mulki burin su ya bar nahiyar su yayi nesa da sarauta , yayi rayuwa mai cike da baƙin-ciki tare da rashin nasara to ko'ina Mulkin Maradi ya zama na Mammadou . Ga rashin sa'ar su sai ta ritsa da su munafunci shi ai daman dodo ne ubangidansa yake cinyewa , Mammadou ba shi da wata kafar kufcewa daga zargin da yake ciki , Maimonatou kaɗai ita ce ke iya fidda shi ita kuwa bata shirya hakan ba , kafin a raba musu ɗakin da ake tsaron su cikin a cikin sa , babu irin roƙo da magiyar da bai mata ba kan ta tausaya ta faɗi gaskiya , amma tayi funfurus sai yaɓa masa baƙaƙen kalmomi masu cike da raini take yi wanda a lokacin shi basu ishe shi sauraro ba bare yayi hanƙoro akai , nadamar son zuciyar da ya aikata cikin kowanne sa'a guda na sake yi masa dabaibayi . Gimbiya Maimounatou kuwa ? Zuwa yanzu lamura sun fara zuwa saɓanin tunanin ta , dan kuwa har kawo yau da take cika satika uku , sau ɗaya bata ji daga wani nata ba wanda kuma tana da masaniyar tuntuni labari ya je musu , to yaya haka ta kasance mata ? Tana sane ko kowa ya iya kauda idanunsa daga gareta sakamakon laifin da ta riga ta aikata , Abban ta ba zai iya ba , saboda sanin da tayi tauraruwar ta ta ɗara ta kowa haskawa a zuciyar Mahaifin su sumfurin ƙaunar ta kuma mai banbanci ce da ta sauran ƴaƴa , duk kuwa da kasancewar ta ɗiya mace , Tun tana sanya ran za'a buɗo kofa ace ta zo ga Maimartaba mahaifinta yazo ganinta da kansa ,tare da Mahaifiyar ta , daga nan ta san zasu nemi belin ta tana da tabbacin za'a basu idan yaso daga baya sun haɗu a kotu su da mutanen Youssoufa da take jin ba wani nisa shari'ar zata yi ba za'a kawo ƙarshen ta sanin da tayi tasu masarautar ai tafi ta su Youssoufa ƙarfi har ma da dukiya . shiru ya tsawaita babu wani motsi daga iyayen ta . ta sassauko burin ace ko da wani daga cikin tarun yayyunta maza da mafi yawa basu wani cika shiri da ita ba musamman waɗanda suke yan uba , amma duk da haka tana harin ko uku daga cikin ne su zo ko da kuwa ace zasu ƙare mata zagi, ita dai ta yadda su zo su ƙarbi belin ta . Har ta kai cikin ƴan kwanakin nan ta fara burin ina ma da ace ko da wani babba daga cikin masarautar su ne ya zo ganin ta ? ko da ace bai nemi belin ta ba ya jishe ta labari na daga abunda ke faruwa ga iyayen ta da ma masarautar su baki ɗaya da yasa suka yi watsi da ita a cikin wannan maƙasƙancin wajen da yafi dacewa da wajen hora maƙasƙanta daga cikin bayun ta . Jita-jita ya kasance gaskiya domin kuwa a daren ranar Maimartaba sarkin Maradi tare da Hajiya Umma suka dawo cikin masarauta . Da dawowar su bai fi da awa guda ba labarin samun lafiyar Biyamuradi ya kewaye masarautar , inda ake da tabbacin farfaɗowar sa daga magagin ciwo sai dai an yi masa aikin da yasa zai ɗan sake yin wasu kwanaki a can ƙasar India kafin ya warke baki ɗaya ya dawo . Tamkar rana haka masarautar ta ɗauki murna har da ƴan bushe-bushen algaitu na bayyana jin daɗin samuwar lafiya ga Biyamuradin Maraɗawa wanda tamkar hatsarin rasa shi da aka shiga ne ya wanke duk wasu laifukan sa na baya da ake ganin sa da shi tare da haɓɓako da ƙaunar sa a zuciyoyin Al'umma . ruwan ƙiyayyar kuma da ganin aibun sai yayi tsallen alkafira ya wanke Hajiya Mama tare da Mammadou , ta ukun su Maimounatou babu wasu abun aibatawa da ya wuce su lungu da saƙo na birnin na maradi murnar dawowar Maimartaba ake tare da farin-cikin jin cewa Yarima yana samun sauƙi . Siyama wacce tunda Hajiya Umma ta shigo sashin nata da daman ita ma tun bayan faruwar lamarin ta baro ɓangaren gidan su ta dawo ɗakin ta da yake sashin uwar riƙon ta , Ita ta bi bayan Hajiya Umma har zuwa ƙuryar ɗakin ta ta kuma shiga Hidimar abincin Hajiya Umma , tana sauraron duk wasu amsa waya da Hajiya Umma ke yi da 'ya'yan ta da sauran jama'ar ta , da duk dai batu ne kan samuwar lafiyar Youssoufa , cikin wayar ne ta ji Hajiya Umma na lissafa sunayen waɗanda zasu tafi India domin cigaba da zama da Youssoufa na ƴan wasu satika kaɗan nan gaba , ƙannen sa maza biyu kawai ta lissafa bata ji sunan ta a cikin masu tafiyar ba. amma duk da haka zuciyar ta cike take da farin-cikin jin lafiya ta fara inganta ga Mijinta , bayan irin tashin hankali tare da fargabar rasa shi da ta shiga da har ta kai ta ga kwanciya rashin lafiyar sati guda sai da ta fara samun labarin samun sauƙi a gare shi sannan ita ma ta fara gyagijewa . Bayan ta kammala haɗawa Hajiya Umma abincin a can ɗakin ta na ƙurya inda ba wani mai shigar sa cikin bayu sai fa su 'ya'yan ta da kuma makusanta na sosai , fitowa tayi daga ɗakin ta dawo ɗan madaidaicin falon da yake tsakanin ɗakin da sauran manyan faluka ta zauna . Hajiya Umma bayan ta idar da sallah ta ɗan taba abincin sama-sama , sai ta ɗaga waya ta ƙira Siyama , nan take kuwa ta shigo tana rike da hannun Yumna , wacce da shigar su ɗakin ta saki hannun mahaifiyar ta tayi wajen kakar ta da gudu ta faɗa mata akan ƙafafu , Da ƴar dariya Hajiya umma ta ɗago ta tana cewa , " ke zainaba ki ɗagga ni kadda ki ƙarasa min ƙafafu ki sa ni ɗingishi dagga dawowa ta daman yaya lafiyar ƙafar ? Birgima yumna ta sake yi akan ƙafar Hajiya Umma kafin cikin 'yar muryarta mai cike da wayo tace ' Umma na faɗi miki ni suna na ba Zainaba ba suna na Yumna ko Mamaa ? Da murmushi Siyama ta ɗan yi gurfano daga gefe tana ƙoƙarin janye Yumna daga kan Hajiya Umma tace , " Yumna bakya jin magana ko idan baki ɗagga Umma ba gobe ban tahiya dake unguwa . Da sauri ta ɗaga Hajiya Umma ta faɗawa uwar a jiki tana cewa ," kin ka ce wajen Baba na zamu tai ba unguwa ba ? Shiru Siyama tayi bata amsa ba , illa ƙafafun Hajiya Umma da ta fara dannawa a hankali tana mata tausa . Da tausayi a ƙwayar idanun Hajiya Umma take kallon Siyama , sarai ta fahimci yadda Siyamar take a ƙagauce da ta ji halin da Mijinta yake ciki ta kuma ji wani batu kan tafiyar su da aka tsara har da ita a waɗanda zasu ganin lafiyar Youssouf ɗin , sai dai zuwa lokacin tahowar su da Youssouf ya nanata kan cewa kada a taho da Siyama cikin masu tahowa wajen sa , tayi zamanta kawai har zuwa lokacin da Allah zai sa ya dawo yasa aka fasa tafiyar Siyama . Hajiya Umma ta so ƙin amincewa saboda ita tafi ganin dacewar zuwan Siyaman da take matar sa fiye da sauran ƴan uwansa , sannan kuma ita ma Siyamar hankalinta zai kwanta muddin ta gan shi da idanun ta saboda tun a india su na da labarin irin mawuyacin halin da ta shiga na fargabar rasa Mijinta . Sai dai duk yadda ta so Youssouf ya amince da zuwan Siyama ƙi yayi a ƙarshe da ta dame shi ana gobe dawowar su , yana kwance kan gadon sa na asibiti Hajiya Umma da Maimartaba kuma suna daga kan doguwar kujerar da take falon , Hajiya Umma ta sake tada batun zuwan Siyaman , da jin haka yasa Youssouf miƙewa a hankali ya zauna yana ɗan cije baki saboda wajen da aka yanka aka masa aiki a uwar hanjin sa har yanzu bai kai ga warkewa ba cikin kwana biyun nan ne ma yake iya miƙewa zaune da kansa Fuskar sa da tayi fayau ta ƙara yin haske babu walwala , bai yadda ya dubi Hajiya Umma sosai ba yace ," Umma , Dan Allah Siyama kadda ta zou , babu wani alfanu a zouwan na ta . Da ƙaruwar mamakin ta take kallon sa ,muryar ta da ɗan fushi wannan karon tace , " to wai mene ne dalilin ka ? Ina sane fa tunda ka farfaɗo baka yadda kun yi kou da waya ta kirki da yarinyar nan ba dagga ta gaishe ka sai ka ajiye waya , me zai sa ka dunga yi mata haka , ita ai wankakkiya ce bata da wani laifi cikin abunda ya afku . Kan shi ya mayar gefe , muryar sa can ciki yace ," kiyi haƙuri Umma , amma Siyama ma ai macce ce , kaidin macce kouwa abun a gudu ne , hatsarin ta mai girma ne baka sanin abounda ke binne cikin ruhin ta , zahirinta cike yake da ƙarairayi da hilata , Allah kaɗai ya san abunda macce take iya ɓoyewa . A lokacin Maimartaba ya ɗago kan shi daga karatun jaridar Hindustan Times da yake , ya kai duban shi ga Yousouf da yake komawa ya kwanta bayan gama zancen sa , Yunƙurowa Hajiya Umma tayi zata sake yin magana , Maimartaba ya dakatar da ita , fuskar ta a marairaice take kallon sa tana son ya ce wani abu ga Youssouf a lokacin , amma sai bai ce kome ba ya komawa karatun jaridar sa . Ko da suka keɓe shi da ita , ƙorafi ta shiga yi masa kan hukuncin da take tunanin Youssoufa ya yanke wanda bai kamata ba ko kusa laifin da Maimounatou ta aikata ya shafi Siyama . Murmushi kawai Maimartaba yayi ,kafin yace " Ki kwantar da hankali , a ba shi lokaci zuwa lokacin da zai gama dawowa ga nutsuwar sa daga ruɗanin da ya shiga , Macce ai mahaɗin rayuwa ce ga Ɗa Namiji , shi da kansa zai safko . Muryar Siyama ta katsewa Hajiya Umma tunanin da ta faɗa , " Umma babu abunda zan sake yi miki ? Girgiza kai tayi , " babu kome ɗiya ta , sai magana da nake so mu yi da ke , Da sauri Siyama ta gyara zama zuciyar ta cike da ɗokin ko zancen tafiyar ta wajen Youssoufa za'a mata ? tace " To Umma , Da tausasawa a muryar Hajiya Umma ta cigaba da cewa , " Nasan kina son zuwa ki ga jikin mijinki to amma saboda halin da zuciyar sa ke ciki yasa aka dakatar da zuwan naki har zuwa lokacin da zai dawo dai-dai, kiyi haƙuri kin san dai yadda wannan mamagunciyar ɗiyar ta zuba masa dafi a zuci da gangar jiki, to sai a hankali zai koma dai-dai dan ma Allah yayi kwanan sa na gaba da zouwa yanzou sai tashin zance , Allah ya ƙara ɗaura mu akan maƙiyan mu na fili da na ɓoye , kiyi haƙuri kin ji ko ? Da murmushin da ta ƙalato Siyama ta gyaɗa kan ta , tana shafar kan Yumna da har ta fara bacci a jikinta idanunta na kallon ƙasa tace ," Umma Allah ya ƙara girma oumarnin kou abun bi ne a gareni shi kouma Allah shi daɗe shi da lafiya . "Amin ,Amin Siyama Allah shi miki Albarka ya dauwamar da zaman lafiya da fahimtar juna tsakanin ku , Umma ta amsa tana mata duba mai cike da so da tausayi , A zuci ta amsa lokacin da take miƙewa saɓe da Yumna a kafaɗun ta tana barin ɗakin , Lokacin da ta shiga ɗakin ta dake falon tsakiya , kwantar da Yumna tayi a kan gado , a hankali ta zame ta zauna a ƙasa ,hawayen da take riƙewa tuntuni ya samu damar shimfiɗowa da gudu , tunanin abu biyu zuwa uku suka fara mata ƙaraƙaina a zuci . "anya ba jikin Biyamuradin bane babu daɗi shiyasa aka hana ta zuwa ta gan shi amma Umma ke ɓoye mata ? Amma kuma ai ta ji sun yi waya da duk wasu makusanta ta kuma tabbatar musu da samun lafiyar sa . " ko kuma ba ita yake son gani ba matar sa Fatima yace a kai masa ? " kadda dai ace abunda Maimounatou ta yiwa Mijinta ya ɗarsa masa tsanar mata da yasa shi gudun su ? idan kuwa hakane babu shakka ba zata taɓa yafewa ɗiyar Agades ba ,da bayan tsawon shekarun da ta kak-kange ta hana ta damar samun gamsasshiyar soyayyar mijinta , ta himmatu wajen hilatar sa da salon soyayyar ta na ƙarya, tsakanin karya da gaskiya har ya aukawa son wata daban ba ita ba , Bayan kuma ga ta ita da ta ɗauki shekaru wajen ƙoƙarin ginawa kan ta matsugunni kome ƙanƙantar sa a zuciyar sa , ta haɗiye duk wani ɓacin rai ta kawar da kai ta danne tasirin kishin ta , amma sai da lokaci ya gabato mata da zata girbi ladan haƙurin ta , sai mummunan nufin Maimounato ya nemi mayar mata da hannun agogo baya ? Runtse ido tayi tana jin ƙauna tare da tausayin Mijinta gefe guda tsoron sake rasa kulawar da ya fara nuna mata take yi . , tunowa da lokacin rabuwar su taki kaɗan kafin tafiyar sa sashin Maimounatou , yadda ya riƙe ta ajikin sa , irin kalmomin da ya furta mata da suka zama tamkar magani ga wani daɗaɗɗan raunin da take fama da shi a rai , da hakan yasa ta jin kwaɗayin son cigaba da samun makamancin daɗaɗan kalmomin sa ya haka , cikin rashin sanin ta mummunan lamari na gaf da afkuwa musu . Buɗe ido tayi tana karanto addu'o'in samun nutsuwar zuci . Washegari da sanyin safiya saƙo ya isowa Hajiya Umma cewa " Hajiya Mama na mata barka da zouwa sannan kouma tana nan tafe zuwa sashin Hajiya Umman , fuskar Hajiya Umma bata nuna wani yanayi ba na farin-ciki ko saɓanin sa tace "a je a ce tana yiwa Gimbiya Saratu Maraba . Zuwa hantsi misalin ƙarfe tara da rabi hajiya Mama ta iso , ƙarƙashin rakiya bayun ta su huɗu ,waɗanda tun daga falon farko suka dakata , Ita ɗaya ta taka zuwa Falon gaba inda ta tarar da Mairamar sarki tare da Siyama suna karin kumallo , kallo ɗaya Aisha Mairama tayi mata ta mayar da kan ta gefe , Fuskar Siyama kadaran-kadahan ta gaishe ta , ita ma tata fuskar babu fara'a ta amsa tana mayar da ganin ta kan Aisha da tayi tsam daga barin cin abincin da take , kafin tayi magana Aisha ta gaishe ta lokaci ɗaya ta miƙe zuwa cikin ɗakin Umman . Ita ta yiwa Hajiya Mama iso ta shiga wajen Hajiya Umma . Bayan gaisuwa shiru ne ya biyo bayan ɗan taƙaiccen zaman da suka yi kowacce tana saƙa a zuci , kafin Hajiya Mama ta gama auna kalmomin da take tafe da su da zummar ajiye su a muhallan da suka dace tace ," Sai kuma wannan lamari mai cike da sarƙaƙiya ya faru ? Wannan yarinya tayi ƙarƙon kifi , ta ɓata nasabar ta , ai kome kyaun nasabar macce muddin bata da hali kamar zoben zinariya take a hancin alade, shiyasa fa ni ban fiye zaƙewa wajen tsantsame zuri'a tafannin auratayya ba, wannan ƙwarya ta bi ƙwaryar bata cika yin ƙarƙo ba sai ki ga anyi gamdakatar da bara gurbi , amma ɗiyan saraki masu son tsalkin nasaba basu gane ba , ai ga irin ta nan Allah dai shi taƙaita , yaya shi jikin Youssoufa? Ya fa kamata ayi wani abu kan Yaron nan Mammadou sabbada kowa ya shaida sharri ne wannan ɗiya take yi masa . Tunda ta fara maganar Hajiya Umma bata dubi sashin ta ba tana a kishigiɗe yadda take , ɗaya bayan ɗaya kalmomin Hajiya Mama suke sukar zuciyar ta tare da bijiro mata da mummunan fushin da take ƙoƙarin tausa zuciyar ta ta danne kamar yadda ta saba haɗiye dayawa daga cikin munanan abubuwan da Hajiya Mama ta sha yi mata ko a kanta ko akan 'ya'yan ta . Fuskar ta na bayyana fushi mai tsanani ta miƙe zaune lokacin da zuciyar ta gama aiyana mata "shi fa maƙaho bai san ana kallon sa ba sai an haɗa da zungurin sa, " Saratu ki dakata daga waɗannan maganganu naki marasa tushe da makama , shi wawa bai san zuru ba sai ya tsinka , ki sani cewa duk wasu kaidi da makirce-makice hadi da ja'iba da ta'annakin da kike bibiyata da zuri'a ta da shi ina sane , ina sane nasan kome tun kafin yau , na yi miki shiru ne saboda nasan shi munahinci dodo shike , muguntar mutum kuma ita ke kawo hallakar sa har inda yayi zaune yana kitsa sharri, sannan akwai ranar da hadari zai taso tare da guguwar da zata wargaza mugaye . Cikin tsakar idanun Hajiya Mama da ta tsare ta da ido ta kai duba suka yi musayan kallo , Ɗan guntun murmushi tayi kafin ta cigaba da cewa , "Saratu kika ce akwai aibu cikin tsantsame zuri'a ? To ai rashin tsantsame zuri'a yasa kin ka kawo matsayin da kike bisan sa a yau , rashin tsantsame zuri'a yasa kin ka zama muguwar uwa mai kitsa sharri , Matar kirki 'yar Nasaba da ita Miji ke fariya yana ado da ita tamkar rigar silki , amma Annamimiya mai haɗa bakin wuta a tsakal gida ita ke saka shi cikin ɗimuwa ta dauwamar masa da shiga kunya da baƙin-cikin da har abada zai kasa samun farin-ciki da ita . " Ya isa Hajiya Safiyya dan na tako na zou shiyar ki ba shi zai baki damar da za ki ci mutunci na ba , Hajiya Safiyya babu yadda za ki iya da ni , banbancin nasaba da ki ka ɗau shekaru kina ɗaga shi sama kina tutiya da shi bai isa ya sauya mana daidaituwar matsayi ba a cikin gidan nan kuma ko kin ki ko kin so Inkiya ta ita ce Gimbiya Matar Sarki . Tana huci ta miƙe tsaye ta fara taku tace " na zo nan ne dan na sanar da ke ki sa a gaugauta sakar min ɗa ya dawo saboda ina da masaniyar ke kika sa aka cigaba da garƙame shi ba tare da ya aikata laifin kome ba . A tsakanin kwanakin da suka biyo baya Bilal da Ubbo tare da Maigidan ta suka tafi india , washegarin tafiyar su kuma Tafeeda shima ya juyo , saboda yanayin aikin sa da bazai bar shi ya cigaba da zama ba a can . Bayan an gama zaman fada da Maimartaba ya tsawatar akan hana cigaba da batun abunda ya faru da Youssoufa , aka fuskanci abunda ya shafi fada da al'amuran ta kaɗai , A daren ranar misalin ƙarfe takwas saƙon ƙira daga Maimartaba ya riski Tafeeda , babu ɓata lokaci ya cimma turakar Maimartaba ƙarƙashin jagorancin jakadiya . Bayan ganawar da bata wuce mintoci talatin ba Maimartaba ya masa iznin tafiys bayan ya samu duk wasu bayanan da yake son samu daga wajen sa . Duk da cewa Hajiya Mama ce take da turaka a ranar amma kasantuwar buƙatar ganawa da Hajiya Safiya ya taso yasa Maimartaba aika jakadiya ta masa ƙiran Hajiya Umma . Lokacin da saƙon ƙiran ya samu Hajiya Umma tayi mamakin Ƙiran nasa sai kuma ta cika da fargabar ko dai wani lamarin ya afku ? Batun da Maimartaba ya zo mata da shi a lokacin da ta isa turakar sa ya busar mata da maƙwallato , da wani irin yanayi cikin muryar ta tace , " Ranka ya dade amma sai nake ganin rashin dacewar Yarima ya cigaba da riƙon amren ɗiyar nan ta Nigeria , wacce ba'a ma kai ga sanin matsayi da tushen ta ba , Ranka ya dade a duba wannan lamarin ayi duba da yadda wannan ɗiya ta agades tazo da ha'inci ita wacce ma take da tsarkin Nasaba ɗiyar girma , ina ga kouma ita wannan da take tsintattar mage a yadda labari ya iske mu ko a can Nigeria basu da wata nasabar da za'a iya haɗa jini da su , ba'a ma san dangin su ba 'Yan Gudun Hijira ne kaddarar rayuwa tare da maƙirci irin na maƙiyan mu ne kawai ya haɗo kasantuwar su tare da ɗan mu me zai hana kawai a raba wannan Amren ? Cikin tsanaki Maimartaba yake kallon ta har ta gama zantukan ta tayi shiru , "Safiyya , ya ƙira sunan ta yana gyara zaman gilashin ƙara karfin gani idon sa . " Na'am , ranka ya dade ta amsa tana mai kaucewa haɗuwar idanun su , cigaba yayi da cewa "Yanzou ashe abunda ya faru bai isa zamar miki ishara ba ? Bai isa miki nuni da cewa kyaun nasaba bai nuni da kyaun ɗabi'a da cikar mutuntaka ba ? Bai isa sanar da ke cewa halin ƙwarai baiwa ce da ubangiji ka iya bayarwa ga bayinsa tsakanin talakawa da masu kuɗi , masu mulki da bayun su Iyaye kouma su taya wajen ƙarin gyaruwar halayya da taimakon gwargadon irin kyaun tarbiyyar da suka yiwa ɗiyan su . "Nasaba ba ita ke tsalkake mutum daga aikata halin banza ba , shi halin Mutum mallakin sa ne daga lokacin faruwar halittar sa da bai da wata alaƙa da wata Nasaba ko ni'imar rayuwar da zai zo ya taras nan duniya . " Domin ɗiyar Nasaba tayi zalunci bai nufin ɗiyar ƙananun mutane tayi fiye da munin abunda ta aikata mai yiwuwa ne ita ɗiyar talakawan ta bayar da mamaki wajen zuwa da ɗabi'u mafiya kyau wajen ƙwaiƙwayo , wannan ɓangare ne na baiwar Ubangiji kamar yadda na shaida miki , dan haka umarni nake bayarwa kan a tai a zo da ɗiyar da Youssoufa ke amre dagga Nigeria ta kasance ƙarƙashin kulawar mu kafin dawowar Mijinta hakan shine zai nuna cikar ƙima da darajar mu , sam ba dattaku irin namu bane mu bar ɗiyar mutane dauke da amren ɗan mu can a ƙasar su batare da sanin halin da take ciki ba , ba'a kuma sanar da ita halin da Mijinta ke a ciki ba da hakkinta ne ta sani . Hajiya Safiyya da tayi zugum tana jin sabon damuwa na mamayar ta Allah ya sani bata son cigaba da kasancewar yarinyar nan a matsayin surukar ta ita da son ran ta ne Siyama kaɗai ce zata cigaba da zama a matsayin matar auren Youssoufa , ta ƙuta sannan tace , " Ranka ya daɗe a halin da Youssoufa yake ciki yanzou babu tabbacin ko yana son cigaba da zama da yarinyar nan tunda ka ga kou Siyama ai.... " Safiyya ta ban san ki da gardama ba kar kuma ki sakayo ta cikin ɗabi'un ki a yanzou , Youssoufa yana son matar sa duk kouma tunane-tunanen da kike yi kiyi watsi da su domin zai zo miki da saɓanin su , dan haka kamar yadda nace a shirya tafiya a zaɓi mutanen da suka dace cikin matayen da zasu tai Nigeria dole ya zama da na jiki ne sosai zasu yi tahiyar nan , sannan a tanadi kome da ya dace domin zouwa tahowa da ita , a yi kome cikin girma idan ta iso a mata masauƙi a sashin ki kussa da ke daɗa ita ɗin ai ɗiya ce Mai girma a wajen mu , Waziri shi zai jagoranci tafiyar tare da shi da Ɗan Malikin Maradi da wasu zaɓɓaɓu amintattun fada. Kallon ba yadda zan yi Hajiya Umma take bin Maimartaba da shi har ya gama jawabinsa da cikin muryarsa ta fahimci a tsaurare yayi maganar cike da sautin umarta dan haka bata da wani zaɓi sai yin yadda yace , sai ta miƙe a hankali bayan ta ce " Ranka ya dade da yardar Allah yadda kace haka za'a yi . MAIDUGURI-NIGERIA . Fatima , ta ji ya ƙira sunan ta can a ƙasan maƙoshi , "Na'am ta amsa tana ɗago kan ta da ta kwantar a ƙirjin sa , " Ranar da duk za ki haihu tare zamu yi naƙuda kiyi rabi nima nayi rabi kin ji ko ? Murmushi mai sauti tayi tana mayar da kanta ta kwantar "Daman ana yin haka ? Ta tambaye shi , "Nima ban sani ba Fatima , sabbada duk ɗiyana biyu bana wajen lokacin haihuwar su , amma wannan ya furta hakan lokacin da yake kai hannun sa marar ta ya shafa , "tare zamu yi haihuwar sa , ɗiyana ko ɗana zasu safko a hannuna idan macce ce kin san sunan wa zan sanya mata ? A hankali ta girgiza kai yace, "Rahamatullah , sabadda haɗuwata da Mahaifiyar ta Rahama ce mai girma Allah shi yi min , Idan kouma ɗa Namiji ne ?, shiru yayi kaɗan , da yasa ta ɗago kan ta tana leƙen fuskar sa , wani irin farin-ciki kalamansa suka ɗarsa a ran ta ," dagaske yake ita tamkar Rahama ce a wajen sa ? Sumbatar goshin ta yayi a hankali yace " na bar miki zaɓi Fatima ke za kiyi masa zaɓin sunan , wanne suna za ki sa masa ? Hannun ta da yake kan ruwan jikin sa ta matsar ta lalubi hannun sa ta haɗe tafukan su waje guda kafin ta sarƙe ƴan yatsunsu cikin na juna kamar mai raɗa tace " Babana . Hannun Yakaka da ta ji ya taɓa fuskar ta shiyasa tayi firgit tana kirkiro murmushin yaƙe , ganin ta ta mayar inda wasu ma'aurata dake zaune suke ta zuba soyayyar su Mijin sai tarairayar matar sa wacce take ɗauke da ƙaramin ciki yake yi kamar zai tayata ɗaukar cikin ita kuma sai zuba shagwaba take tana daɗa narke masa , wayam ta ga basa nan da alama sun shiga wajen likita . tun zuwan su Asibitin da yau zata fara awu da Yakaka tare da Amnee suka rako ta Amnee ita tayi duk wasu kai kawon da bai cika wahala ba kasancewar Asibitin private ne yasa nan da nan ta buɗe mata file tare da biyan duk wasu kuɗaɗen da aka buƙata sannan aka turo su gurin likitan da zai dunga ganin ta . mata Uku kawai suka tarar da a wajen , biyun tare suke da Mazajen su sai ita da wata mata wacce da gani ba haihuwar fari bace sune kaɗai ba mazajen su a wajen . Soyayyar da ta tarar waɗannan ma'auratan na yi ya taɓa ranta , kewar sa da take ta dannewa kuma ta bijiro mata , baki ɗaya a lokacin , "Falmata meyasa kike kuka ? Kin san fa damuwa zata iya sa ki samu ciwo a halin da kike ciki . Shiru tayi bata amsa ba , kamar yadda hawayen ta ya ƙi tsayawa , a dai-dai lokacin zuciyar ta tayi rauni wajen riƙe ciwon da yake damunta a rai ta hana shi bayyanuwa. " Kiyi haƙuri zai zo ku tafi ,yana son ki dayawa Falmata inshaAllah a gidan ki za ki haihu . " bai taɓa ƙiran mu ba tunda muka zo fa Yakaka , watakila ma ya sake ni bansani ba ni tausayin abunda yake ciki na nake yi ban.. " Youssouf ba zai taɓa sakin auren ki ba ya furta hakan da bakin sa kuma a aikace ma ya nuna ki kwantar da hankalin ki kiyi ta addu'a kin ji ko ? Gyaɗa kai tayi tana share hawayen ta dai-dai da dawowar Amne da ta shiga cikin asibitin yin dubiya , damuwar da take damunta ta ɗan ragu . Da layi yazo kan ta ita kaɗa ta shiga , su ka gaisa da likitar mace ce , ta yi mata duk wasu tambayoyin da aune-aunen da suka dace , bata da matsalar kome dan haka magungunan da yakamata masu ciki su dunga sha kawai ta rubuta mata . Rashin ji daga Youssouf ba Falmata kaɗai yake damu ba , har Khaalty Rahima , Amnee da Prof da kan shi , rashin jin wani bayani ko da na ƙiran waya ne daga Youssoufa ya sa su a tunanin makomar auren sa da Falmata ? Sau biyu Prof da Amnee suna tattaunawa a tattaunawar su ta ƙarshe prof ya yanke shawarar kan cewa idan har Falmata ta cika watanni biyu a gida , zai tashi ɗan aike zuwa masarautar Maradi dan sanin halin da Youssouf yake ciki da kuma makomar auren 'yar su , saboda rana ɗaiɗaiku ne bai ƙiran layin wayar Youssouf ɗin amma bai tafiya , ya zama dole yayi wani abu akai a matsayin sa na waliyyin auren kuma a yanzu shi matsayin Uba yake a wajen ta . Falmata taso a bar ta ta dunga bin Yakaka Islamiyar da ko bayan auren ta da Doctor Hamza bata daina zuwa ba . Da farko Prof ya ƙi yarda domin yace babu iznin Mijinta , tayi zamanta kawai a gida sai dai yadda a kwana biyun take yawan zaman shiru damuwar ta kamar ƙaruwa tayi tun bayan zuwanta awu , har 'yar rama tayi gaba ɗaya bata walwala . daga Yakaka ta tafi islamiyyar da take kusan yini a can dan ƙarfe tara na safe take tafiya sai huɗu da rabi na yamma suke tashi kafin ta iso gida biyar saura . Shikenan Falmata sai ta zama shiru a ɗaki ita ɗaya ƙwal, tun Khaalty Rahima na nunawa Amnee kar ta damu kan ta indai Falmata ce daman tun asali ita ba mai yawan son shiga jama'a bace kamar Baban ta take marar son hayaniya Har ita da kan ta Khaalty Rahima ta fara damuwar saboda sai ta yini a ɗaki abinci ma da kyar take fitowa ta ci , Hajja ce daman mai shiga ɗakin ta dame ta har sai ta fito da ita , ita kuma wannan satin duk tana wajen danginta ana biki bata zauna ba . Dan haka sai Amnee ta sake yiwa Prof maganar shiga islamiyyar Falmata ta sake masa ƙorafin zaman kaɗaicin da Falmatan take yawan yi kar ya sa mata ciwo . Prof yace " zai duba lamarin . Ranar asabat da safe kafin lokacin tafiyar Yakaka makaranta , Amnee ta shiga ɗakin su Yakaka hannun ta riƙe da baƙar leda da kaya a ciki , " Yakaka har kin fara shiri ne ? Amnee ta tambaya tana ɗora ganin ta kan Yakaka wacce take sanya safa a ƙafar ta , da sauri ta ɗago fuskar ta da murmushi tace " Eh Amnee sannu da shigowa , " Yauwa sannu takwara ta furta hakan tana sauƙe ganin ta akan Falmata da take kwance akan gado ta basu baya , Ledar hannun ta ta ajiye a bakin gadon , kafin tace " Fatima tashi ki shirya yau dai ke ma za ki fara zuwa islamiyyar , tun kwanaki biyu na sake yiwa Baa Alaji zancen kin ga ashe an miki register ga Uniform ɗin ki ma da litattafan ki duk kin samu sai tafiya makaranta kawai .. Falmata wacce tunda Amnee ta fara bayani ta tashi zaune tana murmushin da ta zarce da dariya jin ƙarshen bayanin Amnee da sauri ta sauƙa daga gadon tana cewa ," Amnee nagode , nagode Allah ya saka da Alheri ki yiwa Baa godiya , inason islmiyya sosai wallahi . Ta ƙarasa zancen da nufar banɗaki domin watsa ruwa , Yakaka da Amnee suka bi bayanta da kallo fuskokin su ɗauke da murmushi . Sosai fara zuwa makarantar ta ya rage mata damuwa domin kuwa yini suke karatu bata samun damar zurfafa tunani , Yau da ƙafa ma suka taho daga makarantar da yake tazarar tsakani ba mai yawa sosai bace Falmata tace, "Yakaka nafi jin daɗin makarantar nan fiye da Ecole ɗin mu ta Niamey wallahi , "Meyasa ko kin fi gane karatun nan ? " A ah saboda a can ko na tafi ecole tunanin Mama baya bari na gane karatun sosai , Allah sarki Mama ta kusa watanni biyu da rasuwa amma koyaushe ji nake kamar ɗazu ta bar ni . Murmushi Yakaka tayi , "ke da Mama ƙauna ku mai girma ce ai, nima naso Allah ya bani damar yin rayuwa tare da ita ko da ba mai yawa bane da nima na samu ladar jinyar ta da sanadin haka Allah zai bani lada mai yawa . " da kuma za ki so ta dayawa fiye da son da kike mata domin Mama 'yar baiwa ce a cikin yara sa'o'in ta wayon ta daban ne kaifin hankalin ta yafi na shekarun ta . Murmushin Yakaka tayi tana jin kewar 'yar ta na zagaya jinin ta , kewa kuwa mai tarin yawa , Ajiyar zuciya Falmata tayi daga nan ta shiga ba wa Yakaka labarin wayo da iyayin Mama wanda daman kusan rana ɗaiɗaiku ne da ba ta bata wasu labarai da suka shafi Mama . Tun a harabar gidan suka fahimci akwai baƙi a gidan saboda baƙin motoci da suka gani har uku , "yau baƙi ne a gidan ko su waye ? Yakaka ta furta hakan tana bin motocin wajen da kallo , can daga ƙasan ran ta tana fatan Doctor hamza baya cikin su . " To Allah yasa baƙin alkhairi ne , Falmata ta furta hakan lokacin da suke nufar ciki Tun kafin su shiga falon ƙamshin da ya karaɗe illahirin harabar wajen yake basu tabbacin baƙin na girma ne . Da Sallama suka shiga falon , idanun su akan hamshaƙan mata huɗu da suke kan kujerun falon sai kuma Amnee da take a tsakanin su fuskar ta fal fara'a . Ɗan taƙaitattcen kallo Falmata ta yi musu da taimakon gilashin idanun ta ta shaida fuskar Ammi , yayar Biyamuraɗi Youssouf , fuskar ta na nan zane a zuciyar ta kamar yadda munanan kalmomin da suka jefa musu yake rubuce tsaf a cikin kwakwalwar ta , Dan haka sai taƙi tsayawa kamar yadda Yakaka ta tsugunna gaishe su ,duk kuwa da cewa ita ma ta gane Ammi , sai ita ta ratsa ta bayan kujerun falon tayi hanyar ɗakin su . Yadda tayi sam bai yiwa Amnee daɗi ba , dan haka ta ɗan ɗaga sauti tace " Fatima zo nan , zo ku gaisa da surukan ki mana ko baki gane su bane ? Yanzu suka iso . Jaa tayi ta tsaya kafin ta waigo cikin rashin kuzari ta dawo baya kaɗan ta yi durƙuso daga nesa tace " Ina wunin ku ? " Kadaran-kadahan Ammi ta amsa ,"da lafiya lau , tana janye ganin ta daga kan ta Asma'u wacce tun shigowar su take faran-faran cike da kissa tace " tashi tashi ƙamna ta durƙuso ba naki ne ba , ɗaga yayar ki daga durƙusso Mairama . Da sauri Aisha Mairama ta miƙe fuskar ta ɗauke da faffaɗan murmushin ganin Falmata , kafin ta ƙaraso Falmata ta miƙe akan ƙafafun ta guntun murmushi ta yiwa Aisha bata tsaya ba tayi juyawar ta ba tare da ta yadda ta sake duban kowa ba ta nufi ɗaki . " Mama kar ki tafi ki barni ki jirayeni Mama , nan ina ne muka zo Mama ? Chak ta tsaya a bakin ƙofar ɗakin zuciyar ta na sauya bugu wannan muryar ta Mama ce , Mama ce take ƙiran ta , da kitsima hakan cikin ranta ta juyo da sauri laɓɓan bakin ta na ƙiran Mama . Idanun ta suka sauƙa kan 'yar yarinyar da bata kai Mama a girma da wayo ba sai tsantsar kamanni da take yi da Mama , tana kokawar riƙe hannun Mamar ta da suke sauƙowa tare daga ƙafar benen a tare Khaalty Rahima na bin su a baya , "Yumna Ta ƙira sunan ta da ƙaramin sautin da bai hana Yumna ta jiyo ta ba , a hankali ta ɗora ganin ta kan ta tana wara manyan idanun ta masu cike da wayo , sai ta sake matsawa jikin mamar ta tana riƙe hannun ta da kyau lokaci guda ta haɗa da maƙale kafaɗa . " Yumna ki je wajen Mamar ki tana ƙiran ki , Siyama ta furta hakan tana ƙoƙarin zare hannun ta daga cikin na Yumma , A hankali Falmata ta ɗaga idanun ta ta ɗora ganin ta kan kyakkyawar doguwar matar da take tsaye gaban ta tana jifan ta da tsadaddan murmushin da yake sake fiddo zallar kyau da wayewar ta , ba sai an faɗa mata ba ta fahimci ita ce Mahaifiyar Yumna , kenan wannan ce Siyama matar Youssouf tuno da matsayin da suke kai a wajen juna ya sa tayi saurin juyawa ta ɗaga taku tana barin wajen , zuciyar ta cike da tunanin abunda ya kawo su haka ? Ko sakin nata aka zo kawo mata tare da matar tasa ? Karɓa irin ta girma da girmamawa ita iyalan Maimartaba suka samu daga wajen Prof da nasa iyalan , duk kuwa da cewa ba'a san da zuwansu ba , hakan bai hana a shiga hidima da su ba ka'in da na'in babu ƙyashi Prof ya buɗe bakin Aljihu aka shiga hidima da su kamar daman can an san da zuwan su dan haka basu tarar da gidan tare da wata alama ta ƙasƙanci ba . Gidan Attajiri suka tarar da ya matuƙar birge su a matsayin gidan su Matar da Youssoufa yake aure , duk sai jikin Ammi da Asma'u '( yar Hajiya Mama ) yayi sanyi da daman su biyun ne suka zo da wata manufa ta daban , sai suka ga ko su sai dai su gwadawa gidan su Falmata sarauta amma ba dai su ƙasƙantar da su ba . ( Daman Bare-bari ai ba daganan ba indai fagen bajinta ne ) . Tunda Falmata ta shige ɗaki bata fito ba a ciki tayi sallar ta ta magarib da isha'i ta hau gado ta lulluɓu bayan ta kashe wutar ɗakin , ta rasa takamaimai halin da zuciyar ta take ciki , farin-ciki ne ko saɓanin sa ? "watau sai yau ya waiwayo ta ? Bayan yasan ya mata laifi , yasan cewa dole tana jiran sa , yasan kuma a halin da take ciki da halin da ta baro wajen sa a ciki . Can ƙasan ranta kuwa , So take ta ji ko da tashin ƙamshin sa ko kuwa amon muryar sa dan ta san cewa ya zo amma ko alama bata ji ɗuriyar sa ba a gidan . Sai juye-juye take yi akan gadon , juyi ta sake yi lokacin da taji an turo ƙofar an shigo gami da kunna wutar ɗakin haske ya gauraya da sauri ta miƙe zaune bayan ta yaye mayafin da ta rufu da shi , Khaalty Rahima ta gani a tsaye a bakin ƙofa , daga inda take tana iya hango ɓacin ran da yake shimfiɗe kan fuskar ta , " Mama sannu da shigowa . Khaalty Rahima bata amsa ba sai da ta ƙaraso kusa da ita , sannan tace " me kike a ɗaki ke kaɗai ? Kina sane da baƙin da suke gidan nan domin ki suka zo , "yan uwan mijin ki ne na jini , wai me yake damun ki ne ? Aina kika koyo wannan mugun halin na walaƙanta mutane ? A ɗan tsorace Falmata tace , kiyi haƙuri Maman mu , un daman ai naga Yakaka tana wajen su suna hira . Daƙuwa Khaalty Rahima tayi mata da hannuwanta duk biyu , " kin ci gidan ku Falmata, dangin Mijin Yakaka ne ko naki ? To bari na faɗa miki gara tun wuri kiyi watsi da wannan banzan halin ki daina dan kuwa ba inda zai kai ki , Mijin ki ɗan Manyan mutane ne gaba da baya ɗan sarauta ne shi da 'yan uwan sa halin girma da girmamawa cikin sa suka taso , shi aka saba gwada musu , muddin kika ce zaki je musu da saɓanin sa ke ce za ki sha wahala kiyi baƙin jini a wajen su ba ke ba har ya'yan da zaki haifa musu . Shigowar Amnee bai sa Khaalty Rahima ta tsagaita ba ta cigaba da cewa , " ki tashi ki shirya ki fito kije ki gaishe su da kyau da kyau biyu daga ciki yayun mijin ki ne ɗaya kuma ƙanwar sa ce ƙaramar su , ɗayar kuwa kishiyar ki ce nasan ba zaki gagara sanin cewa 'yar uwar sa bace da suke 'ya'yan Mace da Namiji dan haka gara ki nutsu kiyi hankali ki daina wannan futsancin naki da tsagerancin wofi ,idan ba ma Allah yayi ba ina ke ina su ? Unm, unm , unm Rahima banda gori kuma , ai shi arziƙi da ɗaukaka na Allah ne , amma 'yata ke ma baki kyauta ba baƙon ka ai abun girmamawa yake a wajen ka , bare kuma waɗannan da suke tafe tun daga wata ƙasa musamman domin tafiya dake , ki shirya kije ku gaisa har can falon Baa Alaji za'a raka ki akwai Manyan mutane da suka zo tare ɗaya daga cikin su Baffan Maigidan ki ne kuma shine waziri garin su sai kuma wasu manya daga wajen su dan haka kiyi shiga ta kamala sosai ko na shirya ki ? Sai a lokacin Falmata ta ɗago kanta da hakan ya bawa ƙwallar idanun ta da suka taru damar zubowa faɗan da Khaalty Rahima ta mata ya haɗu mata da tasowar miƙin irin cin mutuncin da 'yan uwan Youssoufa suka masu a Niamey da yana daga cikin dalilan da yasa ta bar shi wutsiya a zage. Muryar ta na rawa tace " Maman mu da Amnee ku yi haƙuri ku yafe min , amma ni bazan koma ba. Kallon da suka bita da shi bai sa ta tsaya ba cikin kuka ta cigaba da cewa " 'yan uwan sa basa sona zagin mu suka dunga yi suna min gori har iyayena suka aibata sun ce ɗan uwan su ya sake ni me zai yi da ni 'yar gudun Hijira 'yar matsiyata Mama har cewa suka yi ... " Khalass Amnee tace tana zama a gefen ta ta riko ta zuwa jikin ta , kukan da take yi ya taɓa ran su sun kuma fahimce ta , daman Khaalty Rahima ta riga ta san akwai wani dalilin da yasa falmata ta yi mu su yadda tayi , tasan halin 'yar ta Falmata mutum ce mai zuciya da gudun raini , ko kusa bata yadda a taka ta ba tare da ta rama ba . Amnee ta cigaba da cewa "Ko ma me suka ce miki ai ga su dai yanzu iyayen su sun taso su da aiken zuwa su koma da ke cikin girmamawa saboda kin riga kin zama wata ɓangare na jikin su , kiyi haƙuri ɗaukaka bata zuwa a sauƙaƙe , sai an zage damtse an ware ƙwanji wajen neman ta an kuma haɗa da haƙuri da juriya , wa ya faɗa miki inda samun ɗaukakar ka yake zai kasance kewaye da masoyan ka ? Ai ɗaukaka mai tasiri ita ce wacce aka ratsa tsakanin maƙiya wajen samun ta . " ki zama jaruma Fatima-zara gidan sarauta kike aure , Yarima kike aure watarana idan da rai Matar sarki za ki zama dan haka saurin fushi ai ba naki bane . "Sau da dama akwai wuraren da fushi baya yin tasiri sai fa saɓanin sa watau kwantar da kai da kawaici , hannun da ya juri miƙo maka gorar duma kana shan ruwan ciki da ɗaci , sannu kan hankali watarana shi zai miƙo maka gorar zuma tattaciya ka kwankwaɗa daga zaƙin ta , muddin kayi haƙuri saboda kome na duniya ɗan haƙuri ne kiyi haƙuri ki maida kome ba kome ba , kin ji ko ? Gyaɗa kai tayi tana share hawayen ta , zuciyar ta taji tana sanyaya daga ɗacin da ya cunkushe mata rai , ko ba kome yau sun tako sun ga tushen ta inda Mahaifiyar ta ta taso gidan wanda yake matsayin Mahaifi a wajen su , sun kuma san cewa ita ba walaƙantatciya bace har irin yadda suke zato tare da yin iƙirari , daidai gwargawdo Prof ya zama inuwar fakewar su . " shiga wankan maza ki fito na shirya ki kin ji ko ? Amnee ta sake cewa hakan lokacin da Khaalty Rahima ta juya tana barin ɗakin . Da taimakon Hasken da yake falon tar kamar rana Siyama ta ɗora ganin ta akan Falmata wacce tun kafin ƙarasowar ta wajen ƙamshin sassanyan turaren wutan da Amnee ta turare ta da shi iri daban-daban da kuma humra ya ratsa ƙofofin hancin su . 'yar ƙibar da tayi bai sa takun tafiyar ta mai kyau sauyawa ba , tana shirye cikin turarriyar koriyar lafaya mai adon manyan furanni launin jaa mai duhu , da ta naɗa ta akan wata doguwar rigar atamfa mai launin kore mai haske tayi ɗaurin ɗankwali sassauƙa fuskar ta babu wata kwalliya sai ɗan kunnen ta dogo ruwan silver da ya amshi 'yar zagayyar fuskar ta mai ƙaramin kyau . fuskar ta ɗauke da 'yar madaidaiciyar fara'a ta ƙaraso . Yanzu ne ta ga Fatima-zahra sosai , sai dai bata hango abu guda da ya razana ta game da ita ba da ya wuce yarintar ta , ko ba a faɗa mata ba ta ga alamu da dama a bayyane yarinya ce ɗanya da bata wuce shekaru goma sha tara zuwa ishirin ba da in kuwa hakane a kiyaste zata iya girme mata da shekaru aƙalla takwas zuwa tara , ba shakka tauraruwar ta zata daɗe tana haskawa . Murmushi tayi lokacin da take miƙewa , kafin falmata ta ƙarasa durkuson da take shirin yi ta ɗago ta , ɗago kan ta Falmata tayi suka yi musayar kallo kowaccen su da taƙaitatcen murmushi akan fuskar ta , " Kul ki daina yawan durƙuso ƙamna ta , so kike ki yiwa ɗiyan mu lahani ? Ƙaraso ki zamna ni na amshi durƙuson na gaishe da yayun mu , Hannun ta ta jaa suka ƙarasa kujerar da ta taso daga kai , maimakon Falmata ta zauna akan kujerar da take mata nuni sai ta zauna a ƙasa ta shiga gaishe da Ammi da Asma'u da suke bin su da kallo , suka amsa mata kamar ɗazu a taƙaice suka ɗora da tambayar ta lafiyar jikin ta ? Murmushi tayi bata amsa ba . Ta waiga ga Siyama wacce take kallon ta fuskar ta cike da murmushi , "sannu ku da zuwa Mamar Yumna yaya hanya ? "lafiya lau Fatima ƙamna ta da fatan mun cimmuku ƙalau ? "Lafiya . Falmata ta amsa mata a ɗan taƙaice , a mutunce suka gaisa da Aisha Mairama . Shiru ya ɗan biyo baya kafin Asma'u ta juya ga Amnee da son jin ƙarin bayanin da take mata kan haɗin wani turarurruka ( humra )na musamman da matan N'Djamena ke amfani da shi a sassan jikin su da tun shigowar su Amnee ta tare su da tururrukan humran launi-launi cikin wasu 'yan ƙananun kwalabe da aka jera su akan ɗan wani faranti na musamman , ta basu suka shasshafa da daman haka al'adar su take na tarar ɓako da turare musamman idan baƙon na girma ne , Ƙamshin sun yiwa Asma'u daɗi kamar yadda ruwan turaren da kansa ya burge ta launi-launi gwanin sha'awa ga turaren ya zauna musu a jiki ko yaya suka motsa ƙamshin sake tashi yake .shine take son sanin yadda ake harhaɗa su , Amnee kuwa tayi alƙawarin koya mata . Ita kuwa Ammi takaicin Siyama ne fal ya cika mata rai cikin ran ta cewa take "haba me ake da lusaranci irin na Siyama ? Yanzu kishiyar ce abun tarairaya da gatatawa ya haka ? Tun a can ta so a hana Siyamar tahowa saboda ita bata ga dalili ba zuwa bikon kishiya , amma Siyama ta kafa naci har da yin fushin da guntuwar ƙwallar ta , ganin haka yasa Umma amincewa aka taho da ita domin da farko ita ma ƙin amincewa tayi da tafiyar ta Siyama . " en loi kin yi kyau sosai , ƙwalliyar ki ta burge ainun . Mairamar sarki ta furta hakan lokacin da take baro inda take zaune ta dawo kusa da Falmata ta zauna , gani na farko da ta yi mata ta ji ta burge ta ,tana ƙaunar ta musamman da ta gan ta yarinya kamar ma zata girme mata . "Nagode , Falmata tace tana 'yar dariya idanun ta ta sauƙe kan Yumna da aka mata Shimfiɗa da wani lallausan bargo daga gefe tana ta baccin ta da alamun gajiya a tattare da ita , " tayi bacci ne ? tace da ƙaramar murya , Murmushi Siyama tayi tana cewa "ɗiyar ki tayi baccin gajiyar hanya bata saba ba , ga shi kouma baku ko gaisa ba da alama dai yau a ɗakin ki zata kwana da dare idan ta farka kun gaisa ... "Da gaske ? Falmata ta furta hakan tana dariya cikin zumuɗi ta ɗora da cewa "bata ƙuiya sosai ko ? Ba zata yi rikici ba ko ? Tunda bata sanni ba Bana so tayi kuka . Siyama tana murmushin jin daɗin ganin zallar ƙaunar 'yar ta a fuskar Falmata tace " A haka zaku saba ai 'ɗiya ba ta ƙi mamar ta ba... Kafin ta ƙarasa faɗin abunda tayi niyya Muryar Ammi ta katse mata zancen ta ta hanyar cewa . "So kike tayi ta ihu kenan ? Wannan ai ɗaukar hakki ne ki bar 'yar ki a katarar ki sai yafi alheri . Shiru wajen yayi na ɗan wani lokaci kafin muryar khaalty Rahima ta ratso wajen fuskar ta da ɗan murmushi tace " gaskiya kam bare ga baƙunta ga baƙuwar fuska abun zai zama bibbiyu , gara ta zauna a wajen Mamar ta cikin Alheri . " Yakaka da ta lura da sanyin da jikin Falmata yayi sai tace " Falmata da son yara kike wallahi, anya ma kuwa za ki yarda a ɗau naki , zamu gani ai lokaci kaɗan ya rage ke ma ki riƙe naki a hannu inshaAllah . Mairamar sarki ma da abunda yayar su ta ta so yi ya ɗan sanyayar mata da jiki sai tace " ai kuwa ni ce mai raino dole ma ta ba mu ɗan mu ko 'yar mu ko mon beau-père ? Dariya Siyama tayi tana waskewa hararar da Ammi take jefo mata ta ƙasan ido tace " ɗakina ai nan ne wajen ajiyar kayan sa , ni zan dunga shirya shi , kafin a yaye shi daga an yi yaye kuma zai dawo wajena gabaɗaya sai dai Mamar su ta kawo mana wasu kuma . Amnee ce katse musu hirar da suke yi lokacin da ta ce , " Aisha raka ta ta gaishe da baƙi a sashin Baban su . Bayan dawowar su daga gaishe da su waziri Falmata bata tsaya a falon ba ta musu sai da safe kawai ta shige ɗaki , tana warware lafayyar jikin ta zuciyar ta na ga tunanin bata gan shi ba ,Ina yake ? ko dai bai zo bane ? Gabaɗaya sai ta nemi ɗan farin-cikin da ta tsinci kan ta ciki ta rasa da daman zuwa yanzu ta fahimci kusanci da shi da ta samu sanadin ganin 'yan uwansa da zaton ta tare suka zo zata gan shi shine ya sata murna . A yanzu kuma da ta fahimci bai zo ba duk sai ta ji ƙunci na safko mata wani sashi na zuciyar ta taji yana raɗa mata , " Falmata ke fa kike damuwa da shi dan rashin zuciyar irin taki , shi bai damu da ke ba tunda ga shi ya ƙi zuwa wajen ki sai wasu ya turo wai su tafi da ke sai kace wata kaya , zuwan nasu da bai wani burge ta ba , a gurin ta da shi kaɗai tal yazo , ta gan shi suka yi komawar su tare da hakan ne zai sanyata farin-ciki akan waɗannn da aka turo ga shi tun a gaban iyayen ta ma wannan yayar ta shi sai wani hararar take , ko meyasa ta tsane ta ? Oho . Mts Tayi tsaki lokacin da take zama bakin gado , tana ƙoƙarin ture tunanin sa dake damun zuciya da kwakwalwar ta . " Falmata na , ai damuwa kuma ta ƙare tunda ga 'yan uwan sa sun zo tafiya dake , za a mayar da ke gun angon ki mu huta da jin kukan ki da ganin ƙuncin ki "oh su soyayya manya . Yakaka ta furta haka da dariyar tsokana lokacin da take ƙarasowa cikin ɗakin , Yamutsa Fuska tayi ta kawar da kai gefe kafin tace " waye yake cika miki kunne da kukan Yakaka bana so . "Rabu da ita en loi , jibi war hakka kina cikin masarautar mu bayun ki na miki hidima daɗa ai ke ɗin sarauniya ce matar Yarima , Murmushi su duk biyun suka yi da ganin shigowar Aisha da ta cigaba da cewa " kun yi waya da Biyamuradi ko ? Ya jikin na shi da sauki kou ? Ni dai nan tunda munka tasso da mun ka baro shiyar ƙasar mu Téléphone carte sim pas de service . A hankali Falmata ta ɗago kanta zuciyar tana sauya bugu , da wani yanayi a muryar ta tace " Daman ba shi da lafiya ne ? Me ya same shi ? Da sauri Aisha ta dafe kai tunowa da tayi da farkon zuwan su a can falon Prof bayan Waziri ya yiwa Prof taƙaitatcen bayani kan rashin lafiyar Youssoufa da shine dalilin da ya kawo jinkirin zuwan su , amma zuwa yanzu lafiya ta fara samuwa gare shi da yardar Allah , a ƙarshe suka daɗa neman afuwa tare da neman iznin tafiya da Falmata a gobe . Prof ya jajanta musu sosai ya kuma yi musu addu'o'i sannan sai shima ya shigar da neman Alfarma kan a ƙara masa kwana guda tal a bar tafiyar tasu zuwa jibi , sannan kuma ya nemi da a sakayawa ita Falmata batun rashin lafiyar Mijinta tunda bata riga ta sani ba saboda halin da take ciki da ba'a son abunda zai tada mata da hankali . A take duk suka yi Na'am da shawarar Prof kan cewa za'a rufe rashin lafiyar Youssoufa har sai Allah ya masa dawowa sannan kuma zasu ɗaga komawar su zuwa jibi . "Aisha daman Youssouf jinya yake ? Yakaka ta tambaya tana dafa kafaɗar Falmata da ta lura ta shiga damuwa sosai . Da ƙoƙarin sauya akalar zancen Aisha tace " eh ,Ah ah ba wani ciwo bane ya dai tafi india ne , kai Mutanen Maiduguri kun ji daɗin ku ko'ina turaren wuta yana ci Ta ƙarasa zancen tana musu nuni da ɗan burner da take cin turaren wuta a hankali . " yayi tafiya ? Kuma kika ce ba shi da lafiya ne , dan Allah ki faɗa min mana , Falmata ta furta haka tana jin wani gagarumin tashin hankali na rufar mata , muryar ta har 'yar ƙyarma take yi . Da sauri Aisha ta zo gefen ta ta zauna , ta dafa kafaɗar ta sannan cikin taushin murya da alamar rarrashi tace , " en loi kadda ki damou Biyamuradi ya shiga haɗarin rayuwa ne Amma Allah ya fidda shi , doumin kouwa yanzu yana samun lafiya sosai , cikin watan ga mai kamawa shi ke dawowa da yardar Allah kin ji kou ? Gyaɗa kai kawai Falmata tayi daga haka ta miƙe daga tsakanin su , su duk biyun da kallo suka rakata har ta shige banɗaki . Yakaka ta sauƙe ajiyar zuciya tana dawo da ganin ta kan Aisha , cikin yin ƙasa-ƙasa da murya tace . "amma ciwon da yake damun sa ba mai tsanani bane ko ? Ita ma cikin raɗa Aisha tace " ya fa fara samoun sauƙi nima dai baƙina ya subce min . Miƙewa tayi tana ƙarasa cewa " bari na kouma ga masauƙin mu daman na tou yi muku sai da sahe . " ku huta gajiya Aisha mun gode , Yakaka ta furta hakan da 'yar dariya ganin yadda duk Aisha ta ruɗe da ganin sauyawar Falmata . bayan ta fita a sarari Yakaka tace "Hmm indai wannan 'yar rigimar ce ba ku ga kome ba . " wa kenen ? Falmata ta tambaye ta lokacin da take takowa cikin ɗakin kai tsaye ta nufi ɗan saƙon da suke yin Sallah ta hau Sallaya bayan ta zura dogon Hijab har ƙasa ta fara haramar tada iƙhamar sallar shaf'i . " Ni kaɗai nake zance na Yaa Falta . Yakaka ta furta hakan tana miƙewa ita ma ta tafi ɗauro Alwalar ta . Washegari tun asuba masu aiki suka shiga hidimar abincin Baƙi Amnee da Khaalty Rahima basu zauna ba suna tsaye a kan su suna sa hannu a inda ya dace suna kuma gwada musu . Kafin ƙarfe takwas illahirin harabar gidan har maƙota ya ɗau ƙamshin girki da sumfurin ƙamshi iri-iri na daga sunadaran ƙamsasa girki na mutan N'Djamena . Mutan Niger sun ci sun gyatse sun kuma yaba sun zuba santi ba kaɗan ba domin kuwa Ɗan Malikin Maraɗi Mai ruwan kuɗi lokacin da ya gama ƙurbe shayin da aka cika masa 'yar butar shayi ( kettle ) cewa yayi " shi kuma wannan ruwan me sunan sa ? 🤔 ga shi dai yana wani zaƙi-zaƙi kamar tattaciyar zuma farar saƙa , ga kuma wani tsami-tsami da yake yi kamar matsatsen ruwan ɗan itaciyar inabi , ga kuma wani garɗi-garɗi da yake kamar ruwan zam-zam , ƙamshin da yake tashi a cikin sa ai mai samar da nutsuwa ne irin wannan idan kana shan sa kullum ai ka tsufa da ƙarƙon ka 😂 Amnee bata zauna ba ita ta shiga gyara Falmata ta sake goge mata jiki da sauran kayan gyaran jikin Amare da ya rage , kasantuwar bata iya zanen fulawa ba hakan bai hana bayan ta gama murjewa Falmata jiki ta kama kwaɓa lalle da turarurrukan ƙunshi irin nasu bayan ta jiƙa ganyen 'yar itaciyar "Sofan " ta ɗiga ruwan sa da yayi jawur a ƙwabin lallen ta ɗan ajiye shi ya jiƙu kaɗan ta kama ƙafafun Falmata ta rangaɗa mata lallen gargajiya a tafin ƙafar da kan yatsu . Sha ɗayan rana Hajja ta iso da daman tun jiya Amnee ta ƙira ta a waya take sanar da ita batun zuwan dangin Mijin Falmata da zancen komawar su . Da gama wayar su Hajja ta hau shiri ran ta cike da farin-cikin jin cewa Uwarɗakin zata koma ɗakin ta , daman bikin ya ƙare dan haka yau tun safe ta bi dangi ta yiwa kowa Sallama . Prof ya nemi ganawa da Amnee tare da Khaalty Rahima bayan sun amsa ƙiran su ya tambaye su kan me da me ake buƙata da Falmata zata tafi da shi ? Amnee tace " Baa Alaji ai lokaci ya ƙure na yin wani babban shiri sai dai kawai za'a ɗiba mata su turaren wuta a cikin na 'yar uwar ta .. "Meyasa ita baza'a mata nata ba kada a taɓawa 'yar uwar ta kayan ta . Prof ya katse ta , cikin kwantar da murya Amnee tace " to ai lokaci ne ya ƙure yau ne fa kawai ? Idan aka ɗibar mata kaɗan na Amfani idan ya so bayan sun tafi sai nayi waya can N'Djamena ayi mata nata a kuma ƙarowa Takwarata nata a tsanake idan Allah ya sauƙe ta lafiya sai mu tafi mata da kayayyakin ko kuwa ? Ta tambayi khaalty Rahima . "Hakane Ukhtee , Prof ya ce to kayan ɗaki fa da na Amfanin gida ba za'a sauya mata wasu ba ? "duk su ma idan ta haihu sai a mata sabbi tunda yanzu tafiyar ba ta shiri bace . "Hakane to Allah ya kai mu kafin lokacin duk za'a tanadi kome ko ke da kan ki sai ki tafi Dubai yi mata sayayya . Godiya mai yawa Khaalty Rahima ta yi masa bai amsa ba sai cigaba yayi da cewa a cikin ku biyun waccece zata raka ta ? 'Yar Dariya Amnee tayi kafin tace " da wai ni cewa nayi ko Zainab ma tunda ita take kusa anan sai ta kawo yaran idan Mijinta ya yarda sai su tafi tare tunda ga Hajja da daman tare suke , idan ta haihu mu sai mu je . Cike da Amincewa Prof yace "wannan shawara ce mai kyau bari zan ƙira shi Maigidan Zainab sai na nemi iznin sa da kaina , Allah ya kai mu . " Amin Amin , Amnee ta amsa cike da jin daɗi Bayan fitowar su daga sashin Prof a harabar gidan suka ci karo da Yakaka sai kai-kawo take a mamakance Khaalty Rahima tace " ke kuma me kike yi anan ? Da sauri ta matso tana riƙo hannun Amnee ta ɗan rangwaɗa kai sannan tace " Amnee Dan Allah zan raka Falmata Niger ɗin ? Bana son ta tafi ita kaɗai nasan duk takura zata yi a tsakanin su tunda basu wani saba ba . Kallon kin cika sakarci Khaalty Rahima ta mata kafin tace " Da iznin wa za ki tafi ? Kin san dai da Auren ki idan kuma gaban kan ki za kiyi to , Mayar da ganin ta tayi kan Amnee ta cigaba da cewa " Ukhtee mai sunan ki dai sai kina yi kina taro ta sam bata da wayo . Daga haka ta shige ciki ta bar su a tsaye , Amnee ta dubi Yakaka fuskar ta cike da murmushi tace ," takwara kema ai Amarya ce duk yaushe aka yi bikin ki ,? Ki bari idan ta haihu sai mu tafi tare . " Amnee kawai raka ta zan yi fa Wallahi tausayin ta nake ji ace ta sake tafiya ita ɗaya , sai Hajja . " Zainab ma zata raka ta . Ta katse ta . Zata sake yin wata maganar Amnee tace " ki tambayi iznin Mijin ki idan ya bar ki sai ku tafi tare . "Ɗan tsallen Murna Yakaka tayi ta ƙanƙame hannun Amnee da yake cikin nata tana cewa "Nagode , nagode Amnee naa . A hankali Amnee ta zare hannun ta ta wuce ciki tana dariyar rashin wayon Yakaka , ita yanzu idan an bar ta sai ta sake kwasar ƙafa ta bi Falmata ita bata tunanin gina nata gidan auren da har yanzu bata da takamaimai matsugunni a cikin sa ? Ita kenan kome na rayuwar ta zai biyo bayan uzurin Falmata ne . Jinjina kai tayi cikin ran ta ta kasa ƙiyasto iya adadin girman ƙaunar da Yakaka take yiwa Falmata , can sashi guda na ranta dariya take dan tasan ko kusa Hamza ba zai Amince da tafiyar Yakaka Niger ba bare kuma Prof . Bayan wucewar Amnee Yakaka tsumu tayi a tsaye , ita sai yanzu da aka ce ta ƙira Doctor Hamza ne ma ta tuna ko number sa bata da ita a wayar ta , gaskiya tana son raka Falmata Niger ɗin nan saboda ko a hanya wannan ƙatuwar matar zata nemi ɓata mata rai ta tare mata . Zama tayi akan dan dandamalin da aka yi shukar furanni ta cikin sa tana tunanin ina zata samu layin Doctor hamza , ita dai ba zata iya tambayar Amnee ba kunya take ji , ba kuma ta son ta tambayi Rahima ko da a waya ne tasan sai ta sille ta ta mata tsiya . Wayar Mamar su ta faɗo mata a rai tasan babu tantama akwai number sa a kai , to ko zata ɗauka ta ƙira shi kawai ma ta wayar ta ta ƙila yafi ɗagawa da wuri fiye da idan ta layin ta ta ƙira da bai san layin ba . Da sauri ta miƙe ta shiga ciki , ta hau sama ɗakin Khaalty Rahima da sa'ar ta babu kowa a ɗakin , daga gefen gado ta hango wayar , da sauri ta ɗauka ta shiga neman sunan sa cikin jerin sunayen dake kan wayar bata sha wahala ba ta samu sunan tare da number sa . Shiru tayi ta gagara danna ƙiran , tana son tattaro kalmomin da zata yi amfani da su wajen yi masa magana , Idon ta ta kai kan agogon wayar ta ga sha biyu saura tasan dai duk tsiya yanzu ya tashi a bacci duk kuwa da cewa yau lahadi ce ba aiki . Fargaba bai rabu da ita ba ta danna ƙiran layin bayan ta kai wayar kunne ta runtse ido gam tana jin wani yanayi mai ƙarfi na shigar ta , daga can ƙasan ran ta addu'ar samun nutsuwa ta fara yi . Wural ta buɗe idanun ta lokacin da ta ji sautin muryar computer na bata tabbacin babu kuɗin da zai isa ƙira a wayar . Dariya tayi da ƙaramin sauti , kafin tace " kai Maman mu sai a bar ta ko meyasa take barin waya ba kuɗi ? Ita kamar ma bata wani damu da wayar ba . Numbers ɗin ta kwafa a wayar ta , sai da ta zauna a bakin gado sannan ta danna ƙiran . ABUJA Daga can Sofiya ce a ɗakin Doctor Hamza tana gyara gadon da basu wani jima da tashi a kai ba Doctor Hamza ya shiga wanka . Tana gyara bargon su lokacin da wayar sa dake gefen gado ta ɗau kiɗa alamun shigowar ƙira . Ba tare da ta dau wayar ba ta leƙa fuskar ta ga lambobi ne reras ba suna , ɗan yamutsa fuska tayi ta gatsina guntun hancin ta kafin tace "yau Sunday ma ba za ku bar mutum ya huta ba shi kenan cikin jigila tsakanin asibiti da gida yau kam rana ta ce sai na more lokutana da aka cinye na sauran kwanaki tsawon sati . Har wayar ta gama ƙara bata ɗaga ba . Daga can Yakaka tayi jim da waya a hannun ta , cike da tsoron kar ta dame shi ta daure ta sake danna ƙiran a karo na biyu , Wannan karon har Sofiya zata fice a ɗakin sai ta dawo baya , ta ɗau wayar kai tsaye ta ɗaga ƙiran tana kara wayar a kunne tace " Hello who's on the line ? " Mukut Yakaka ta haɗiye yawun firgici , jim tayi kafin tace " amm ni ce Yakaka ina kwana ? bata tsaya ba ta zarce da cigaba da cewa "ki kaiwa Yaya doctor wayar . Ba domin Sofiya tana shakkar kar Doctor Hamza da tasan kunnen sa yana iya jiyo ta ba da ba abunda zai hana ta ɗuɗɗurawa Yakaka zagi . Baki ɗaya fuskarta tayi jaa a take tana huci tayi ƙasa da murya kafin tace " To akuya sarkin naci ana ƙorar ki kina daɗa naniƙewa , shugabar 'yan rashin zuciya Miji bai damu da ke ba sai ke ce ke neman sa jarababba , to ƙwalelen ki ke da Doctor sai gani sai hange daga nesa-nesa dan kuwa zaman ki kenan a inda kike 'yar ..... Ƙit ! Ta ji Yakaka ta katse ƙiran , Daɓas ta zauna a bakin gadon baki ɗaya ranta ya cunkushe har wani raɗaɗi take ji a hancin ta kamar ta shaƙi barkono ," wannan jarababbiyar yarinyar watau har ƙiran Mijinta take yi ? " Sofi waye ya ƙira ni naji kamar kin ɗaga wayar ? Da sauri ta waiga kafin ta miƙe tsaye ta ƙarasa zuwa gaban shi inda yake tsaye yana goge kansa da towel , Tana zuwa ta karɓi towel ɗin ta shiga goge masa jiki , bata yarda sun haɗa ido ba fuskar ta babu walwala tace , " Akuya ce ta ƙira ka ? 🙄 "Akuya fa ? Ya tambaye ta yana duban ta da mamaki , Cike da bagararwa ta kai hannun ta ƙirjin sa tana ɗan tsikarin sa tace " eh dan kukan akuya nake ta ji tunda na ɗaga wayar ina Hello , Hello , Hello . Ba'a cewa kome sai Kukan Akuya . Jawota yayi ya haɗe tsakanin su , yana kallon cikin tsakar idon ta yace " Sofi baki fa da kirki a wasu lokutan nasan daga Office ne aka ƙirani , Ni yanzu muje ki bani abinci na ci yunwa nake Ji ina son na fita akwai wani waje muhimmi da nake son zuwa yau . Kicin-kicin tayi da fuska jin cewar zai fita yasa ta sake jin tasowar ɓacin rai da ya ɗan fara lafa mata sanadin haɗuwar fatar jikin su . Bai kula ɓacin ran ta ba yayi shirin sa cikin wani yadi mai ɗan nawi ruwan zuma ya fesa turare tare da ɗaura agogon sa sai lokacin ya juyo ya dube ta da take zaune a bakin gado ta kumbura suntum . Fushinta bai wani taɓa masa rai ba yace " mu je ki bani abincin ba daɗewa zan yi ba zan dawo nima so nake na huta yau ɗaya . Bayan ya ɗan cac-cakali Omelet da kidney Sauce ya ɗan kurɓi ruwan tea ya miƙe a gurguje ya mata sallama yana barin gidan . Da fitar sa ta yi jaɓar ' akan kujera tunanin ƙiran wayar sa da Yakaka tayi ya bata tsoro , ita da ta saki baki ta zauna malumman ta sun ce mata an yiwa Yakaka da Hamza farraƙu to tayaya Yakaka ta iya samun damar ƙiran sa ? Kada dai ace asirin nan bai ci ta ba ? Wani irin huci take yi lokaci guda ta tashi da gudu ta hau sama ɗakin ta ta shige laluben wayar ta , ya zama dole ta sabunta aikin ta .😂 *** Doctor Hamza kuwa yana fitowa hankali kwance ya dai-daita motar sa akan titi unguwar su Malama Maryam ya tasamma da bata kasance ɓaƙuwar unguwa a wajen sa ba , ya sha kai sofiya gidan ƙawar ta Samira . Tsawon sati biyu da yayi yana bin duk wasu Matakai daki-daki domin tabbatar da zancen da Suleiman ya sanar da shi game da Yakaka gaskiya ne ko ba gaskiya ba ? Duk da cewa yana da tabbacin Suleiman ɗin ba zai masa ƙarya ba amma yana da buƙatar samun ƙwararan hujjoji ko dan ya wanke zargin ta daga ransa da hakan shine kaɗai zai ba shi damar samun nutsuwa tare da ita da zai iya rungumar ta hannu bibbiyu , tun usul ƙaunar ta bata tunbuƙe ba daga ransa girgiɗi kawai tayi da a yanzu kuma ta dawo ta tsaya chak da ƙafafun ta ta kuma shiga kaiwa duk wasu gaɓɓan jikin sa mamaya . ASSALAMU ALAIƘUM MASU KARATU . Da fatan duku kuna lafiya ? Sakamakon saƙonnin da nayi ta amsa daga masoya masu karatu kan taƙaice ƙarshen MHR da wasu ke ƙorafi wasu kuma suka nemi Alfarmar na ɗan sake jaan zaren labarin nayi dalla-dalla ko da kuwa ban yi filla-filla ba , hakan yasa na karɓi ƙorafi na kuma ɗan jaa kaɗan ba mai yawa ba da nan gaba kaɗan mu kan iya rufe bangon littafin mu adana shi Insha Allah A ƙarshe ina godiya sosai da sosai ga dukkanin makaranta MHR na fili da na ɓoye daɗa nasan na ɓoyen sun ninka na filin yawa "ghosts readers barkar mu dai ina gaisuwa fa 😜❤nasan kuna tare da ni domin ina ganin inuwar ku , ko da kuwa baku bani tukuici ba . Nagode.    [2/3, 9:34 PM] +234 803 083 8792: Mafari ( Hargitsin Rayuwa ) Umm'muaz 50 Lokacin da Doctor Hamza ya isa unguwar su Malama Maryam dai-dai layi da gidan da Doctor Suleiman ya kwatanta masa sai ya ga ashe ma ya taɓa sanin gidan duk kuwa da cewa da dare ya taɓa zuwa amma bai manta da yarinyar da ya taɓa taimakawa ba a wani dare ana ruwan sama babu shakka a ƙofar wannan gidan ya sauƙe ta . Kasancewar ana haramar sallar Azahar a lokacin dan haka a masallacin da yake kusa da gidan nan yayi Sallah . Bayan ya idar sai ya matsa ya miƙawa Liman hannu suka yi musabaha , nuni ya yi masa kafin ya ɗora masa bayanin gidan da ya zo , to amma kasancewar an sanar da shi matar tana da aure ya zama dole sai da iznin Mijinta zai gana da ita , tunda ba sanin juna suka taɓa yi ba dan haka yake son sanin Mijin ta da farko , a zahiri wata buƙata ce ta son samun wasu bayanai daga bakin Matar da ake ƙira Malama Maryam yasa shi tasowa musamman domin ganawa da ita . Dan jim liman yayi yana sake nazarin Doctor Hamza , kafin yace " bawan Allah lafiya dai ko ? Ba dai wani al'amari bane marar daɗi ya auku da har yasa kake neman Malama Maryam ? Da sauri Doctor Hamza ya girgiza kai kafin yace ' ah ah ba wani abu bane marar kyau , kawai tambayoyi nake so nayi mata akan wata ɗalibar ta da ta koyar wacce aka ce daga baya ta zama kamar 'yar ta saboda kusanci da ta samu da ita , sunan yarinyar Amina . Shiru Liman ya sake yi kafin yace 'Kana nufin Amina Mustapha Dilmari yarinya 'yar Maiduguri ? " ita fa Malam . "Allah sarki yarinyar kirki ce ai Amina , ta koma can garin su a halin yanzu har an aurar da ita sati biyu da suka wuce , Malama Maryam da kake nema ai Mata ta ce , kuma ita ce Malamar Amina tsawon shekaru Shida da suka yi tare , bari na shiga gida sai nayi mata bayani na haɗa ku , amma kafin nan zan so jin ko kai wane ne ? Kuma daga ina kake ? Cike da jin daɗin ganin sauƙaƙuwar lamura Doctor Hamza yace " Malam ai ni ne Mijin Amina bayan haka kuma ni wan ta ne da muke 'ya'yan mata biyu . " Masha Allah ka ce babban baƙo ne da mu , to Bismillah mana mu shiga daga cikin Falona kafin na yi mata magana . Ganawar Doctor Hamza tare da Malama Maryam ya zo masa da wani irin sauyi mai girma da yake sauraren bayanan da take yi  masa game da baki ɗayan rayuwar da Yakaka tayi tare da ita har ma da wanda tayi gidan uwarɗakin ta samy baby da a farko su kayi zaton yayar ta ce , kafin daga baya lokacin da ta faɗa musu haƙiƙanin gaskiyar kome game da ita ,su gane cewa basu da wata alaƙa ta 'yan uwantaka . " alaƙar ta da Samy Baby da duk irin Yaudarar da tayi mata . har yadda daga baya Samy baby take son tilasta ta shiga harkar banza amma ta ƙi yarda da hakan shine ya kawo sanadin komawar ta Maiduguri . Nisawa Malama Maryam tayi tana murmushi ta cigaba da cewa " Abu mafi daɗi da yasa nake yin Alfahari da Amina shine jajircewar ta wajen neman ilmin addini fiye da na boko , Amina ta fara karatun addini bata kai ga sanin ayoyi bakwai na Suratul-Fatiha ba amma sai ga shi cikin shekaru shidda da Yarjewar Allah ta samu cikakkiyar kyakkyawar Haddar izif talatin . " bata san yadda ake yin cikakkiyar Alwala ba a shekaru shidda baya a yanzu Amina daga kan farillai , sunnoni da mustahabbai har makruhi na alwala ta sani , haka kuma sharuɗɗan Sallar ta sun inganta ta kuma san yadda zata yi gyara ga Sallar ta idan ta ɓaci. " Amina ta san baƙi , ta iya karatu da rubutun Arabic ta kuma samu tarin ilmi daga littatafan addini da hadisai masu inganci dan haka ta san dukkanin haƙoƙin Ubangiji dake kan ta . " Alhamdulillah shine kawai abunda zance da Allah ya rataya min nawin tallafa mata ta hanyar samu ilmin addini , ya kuma bani ikon koyarda ita tare da ni da sauran Malaman da ta ɗau ilmi a wajen su , nagodewa Allah da kafin barin ta wajena ta fita daga duhun jahilci . "Halaye da ɗabi'un Amina mafi rinjayen su masu kyau ne ababen koyi , tundaga lokacin da tasan irin tarin zunubin da yake cikin kuskuren da tayi na baya bata sake kwatanta aikata makamancin sa ba , tayi kyakkyawan tuba da irin sa ake son duk wani mumuni ya yi . " babu shakka kayi sa'ar Mata , Allah ya ɗorar da zaman lafiya a tsakanin ku, a ƙarshe shawarata shine kayi ƙoƙarin ganin ta samu cigaban karatun ta na addini kamar yadda ta ke fata a koyaushe watarana ta haddace Alkur'ani Mai girma Dan Allah ka bata dama ka taya ta wajen samun cikar burin ta irin Amina sune Al'umma suke amfana da su . " Ya Rabb lakal-Hamdu ,  Alhamdulillah , Masha Allah . Doctor Hamza yake furta haka fuskar sa ɗauke da wani irin annuri na farin-ciki , har wani irin zillo yake ji zuciyar sa na yi masa . fuskar sa ɗauke da faffaɗan murmushi ya miƙawa Malam Idris ( Mijin Malama Maryam ) Hannu suka yi musabaha , lokacin da yake miƙewa da shirin tafiya , bakin sa ɗauke da duk wasu kalmomin da ake iya amfani da su wajen godiya ga mutumin da ya kai maƙura wajen yi maka Alkhairi . Da farin-ciki su ma suke amsa masa suna masa rakiya , fitowar su tsakar gida ya zira hannuwansa duk biyu a Aljihu , kuɗaɗen ciki da bai ƙirga su ba su ya tattaro baki ɗaya ya danƙawa Sadiq da yake tsaye a gefe cike da ladabi ya sanya hannu biyu ya amsa yana godiya . Sun rabu cikin mutunta juna ya jaa motar sa yana barin unguwar , daga cikin zuciyar sa yake jin ɗaguwar wani abu mai kama da nannauyan dutse da ya danne masa zuciya ya taƙaita masa walwalar sa shekara da shekaru , ji yake kamar an tsamo sa daga cikin wani zuzzurfan ramin da ya faɗa a ciki , yanayin da yake ji bai taɓa tsintar kansa a ciki ba soyayya mahaɗi ce ta rayuwar kowanne ɗan Adam wanda da zarar an samu tangarɗa ta bangaren ta sai rayuwa ta zama kamar lami babu armashi a cikin ta . Tuƙin da yake yi yaji yana neman gagarar sa zuciyar sa na neman abokin taya ta murnar da 'yancin da ta samu , dan haka ya gangara gefen titi ya tsaya , jingina kansa yayi da jikin kujerar motar bai ankara ba ya tsinci kansa da yin murmushi lokacin da ya ji wani ruwa-ruwa na taruwa a gurbin idanun sa ( ƙwallar farin-ciki ) shi kaɗai kawai yake ta murmusawa wanda bai san shi ba wanan lokacin zai zaci mutsa-mutsai ne suka hau kan sa . " Alhamdulillah ,yace yana kai hannu kan wayar da take ajiye a gefen sa ya ɗauka laluben wanda zai ƙira a dai-dai lokacin yake yi , Doctor Suleiman shine wanda ya fara faɗo masa arai domin ya raba farin-cikin sa da shi, saboda sanadin sa ya samu kubta daga ramin da zargi ya haƙa masa a zuci ya faɗa . sai dai tunowa da ya yi da alaƙar da ta taɓa giftawa a tsakanin sa da Yakaka ya sa shi fasa ƙiran sa , daga ƙasan ran sa yake jin tasowar kishin son da Suleiman ya taɓa yiwa Yakaka . Ajiyar zuciya yayi yana jin yadda zuciyar sa ke bijiro masa da wacce tafi dacewa da ya ƙira a lokacin . Tunowa yayi da ba shi da number ta , ba ma shi da tabbacin ko tana da waya,ko babu , shiru yayi jim ! Yana tunanin ina zai samu layin ta ? Yana jin nawin Amnee da Khaalty Rahima ba zai iya tambayar su ba . Rahima ƙarama ita ce ta faɗo masa , yasan muddin dai tana da waya zai samu layin ta wajen Rahima ' Yana ƙiran ta kuwa ta ɗaga , bayan sun gaisa ya ɗan yi gyaran murya kafin yace " Rahima kina da number Mata ta kuwa ? Ɗan shiru Rahima tayi kafin tace " eh Big bro ina da number Auntie Sofiya... " Ba sofiya nake nufi ba Number My Pure Woman nake nema ai tana da waya ko ? Murmushi Rahima tayi lokacin da ta fahimci wacce yake nufi amma dan ta sake tabbatarwa sai tace " number Yakaka ko Big Bro ? "Yakaka ba suna bane ku daina ƙiran ta da wanan sunan ku dai samar mata da wani sunan da ya dace da ita mai daɗin saurare idan ba za'a ƙira ta da Aminah ba. Ya zarce da cewa "ki turo min da Number ta yanzu . bai saurari dariyar da take yi ƙasa-ƙasa ba ya sauƙe wayar sa . Ba'a cika mintuna biyu ba Rahima ta turo number , cikin zumuɗi ya danna ƙiran yana fatan Allah yasa ta ɗaga da sauri . Yakaka wacce tunda ta ji irin zagin da Sofiya ta biyo ta da shi , ta tsorata jikin ta kuma yayi sanyi lakwas daga haka tana iya hango kusancin da suke da shi da Matar sa tunda har tana iya ɗaga wayar sa idan an ƙira , wani sashi na zuciyar ta ma raɗa mata yake cewa duk a gaban sa sofiya ta ƙira ta da Akuya . Hawaye ta ji yana neman zubo mata , ita kam wannan auren nata bata hango jin daɗin sa ba . Jiki a sanyaye ta fito daga ɗakin,  ta sauƙa ƙasa inda ta tarar Amnee na yiwa Falmata ƙunshi a ƙafafun ta da ƴan yatsu zama tayi tana taya Amnee gyarawa Falmata tsaruwar layin ƙunshin , fuskar ta babu walwala sosai tace " Falmata naso raka ki har ɗakin ki , na mayar da ke saboda ni nayi sanadin tahowar ki , amma ban samu dama ba Yaa Dakta bai barni ba , amma insha Allah idan kin haihu zan je kin ji ko ? Gyaɗa kai Falmata tayi da ɗan murmushi tace " Yakaka ai daman nasan Yaa Dakta ba zai yarda ba  Amaryar sa ta kama hanyar ƙasar Niger rairayin ƙasa ya turbuɗe masa ke .. " ki min shiru , Yakaka ta katse ta tana 'yar hararar ta tare da satar kallon Amnee wacce tayi kamar bata jin me suke cewa , Dafe baki Falmata tayi kafin tace "to nayi shiruna Allah ya kai mu. Daga haka tayi shiru daga ƙasan ran ta tana ji rashin daɗi da bata samu rakiyar Yakaka ba saboda duk guri idan har da Yakaka tana jin wata irin kariya ta musamman daga jiki har ruhin ta . Bayan Yakaka ta idar da Sallar azahar tana zaune akan sallayar wayar ta ta fara ƙidan shigowar ƙira . Da sauri ta miƙa hannu ta ɗauki wayar zuciyar ta na ƙirgo mata waɗanda zasu iya ƙiran ta a dai-dai lokacin , number da ta gani ta sa bugun zuciyar ta sauyawa, take zuciyar ta ta bijiro mata da tambayar "me kuma Sofiya ta ƙira ta sake cewa ? Ko cin mutuncin da tayi mata ne bai ishe ta ba ? Har wayar ta tsinke bata ɗaga ba , a take kuma aka sake ƙira , tsoron ta ya sake ninkuwa da ta tuno ko dai shine yake ƙiran nata ? Kar kuma tayi laifi idan taƙi ɗagawa Dan haka kafin wayar ta kai ga katsewa sai ta ɗaga ƙiran a ɗan tsorace ta kara wayar a kunnen ta tayi shiru . Doctor Hamza da ya ƙagauta da ya ji muryar ta ya saita sautin sa ƙasa kaɗan kafin yace " Hello Wafaa , ya kike ? Shiru Yakaka tayi tana son daidaita nutsuwar ta dan ita gaba ɗaya ma a gigice take da jin muryar sa dan haka sai tace " Salamu Alaikum Yaya Dakta , ba Wafaa bace ba ni ce . Shiru ta ji yayi kamar baya kan wayar ɗan dubawa tayi ta ga yana nan akan layin tsoron kar ya kashe wayar ba tare da ta faɗa masa abunda take son cewa ba yasa ta cigaba da cewa " Daman ina so ne Dan Allah..... " Shiiit ki tsaya mu gaisa Wafaa , ko haka ake gaishe da Masoyi? Saƙato Yakaka tayi da wayar tana jin mamakin sa a take tayi tunanin ko dai bacci yake yana mafarki da wata can wai wafaa ? Dan haka cikin sanyin murya ta sake cewa "Yaa Dakta ni ce fa ? Dariyar da take taso masa ya danne yana sake ƙasa da murya yace "  ke ce wa? Kamar zata fashe da kuka tace " Ni ce fa Yakaka yayar Falmata . Murmushi yayi yana rufe idanun sa cikin ran sa cewa yake " tana son sunan nan tana kuma son ƙanwar ta . " sunan ki ba Yakaka ba , sunan ki Amina kin ji ko wafaa ? Shiru tayi , tana son haɗa kalmar da za ta faɗa a lokacin fahimta da tayi zuwa yanzu ya gane ta kawai walaƙanci ne ya sa shi ƙiran ta da wata wai wafaa , ɓata rai tayi kamar yana ganin ta tace . "Ni dai daman iznin raka Falmata Niger nake nema a wajen ka ? 'Yan uwan mijin ta sun zo zasu koma da ita shine zan raka ta . Wani irin bugu zuciyar sa ta shiga yi kamar tana gaban sa ya tattare girar idanunsa cikin muryar sa da bata cika ƙarfi ba yace " Wafaa me kike son cewa ?  Da auren nawa akan ki za ki tafi har Niger ? Ki je ki ga wannan ɗan.... Shiru yayi yana son dawo da nutsuwar sa da kishi yake neman raba shi da shi nan take , da wani irin sauti yace " baza ki tafi ba kina jina ko ? A tsorace tace " ina ji . . "Good . yace kafin ya kashe wayar sa . Wani irin zafi yake ji a zuciyar sa kan cewa da tayi zata je Niger garin su wannan ɗan iskan sojan har cikin gidan sa kuma ? Alhalin da yau yana da iko bayan duk labarin da Malama Maryam ta sanar masa har auren sa da Falmata a halin yanzu ko Fatima ba zata sake kwana da igiyar auren sa ba , tunani ma ya dunga yi kan me yasa Baa ya ba shi auren Fatima ? Alhalin shi ɗin bai can-canta ba . Ko ma meye shi dai zai killace matar sa daga yin duk wata mu'amala da shi ko dangin sa duk kuwa da cewa yana auren ƙanwar ta ba zai jura ba ya ga ko da kalmar gaisuwa ta sake shiga tsakanin su.( anya kuwa likita ayi haka ?? ) Bai bari maganar da ta faɗa ta ɓata masa farin-cikin sa ba saboda zuwa yanzu yasan wacece haƙiƙanin ta , mace ce mai kyautayi da son kyautatawa mai saurin yarda da yawan sadauƙarwa halinta kenan halittar ta ce shiyasa ya raɗa mata suna ( Wafaa ). Abun da ya ɗan so tayar masa da hankali bai wuce rashin sanin matsayin sa ba a wajen ta ? sai dai ya yarda da kan sa shi ai Namiji ne zai iya sauya ta zuwa yadda yake so ya koyar da zuciyar ta ƙaunar sa da hakan shi zai samar da nishaɗi a zaman su tare da taimakon sassanyar zuciyar ta mai cike da tausayi da jin ƙai . Tayar da motar sa yayi yana nufar gida cikin ran sa cike da ƙudirin zuwa Maiduguri a ƙarshen sati mai zuwa ya fara kafa gwamnatin sa tun yanzu kafin nan da ƙanƙanin lokaci da zai dauƙe ta ta dawo kusan sa . Har zuwa lokacin da ya koma gidan ya tarar da Sofiya yadda ya bar ta , sai daɗuwar damuwa da tashin hankalin da yake iya gani akan koɗaɗɗiyar fuskar ta Kamar wacce take jiran sa yana zama ta zo ta zauna a ƙafafun sa tana kaɗa ido tace " Doctor na har ka dawo ? . "Har na dawo Sofi ta daman ai na faɗa miki ba zan daɗe ba . Murmushi tayi tana raɓa kan ta a kafadar sa ta cigaba da cewa " Doctor na bayan fitar ka na yi mana wani tunani , akan yarinyar nan ƙanwar mu Yakaka take ko wa ?  Bata tsaya ba ta cigaba da cewa " me zai hana ta dawo nan gidan ta zauna a ɗakin nan na 'yan aiki kafin a samu wajen da za'a wurga ta tunda kaga fa irin halin ta na cuɗanya da maza ta riga ta saba da 'yan taɓe-taɓe da tsotse-tsotse da kwakule..... " kin ga bana son shirita ki faɗa min magana kai tsaye kawai . Ya furta hakan a taƙaice fuskar sa na bayyana wani yanayi na daban saɓanin wanda ya shigo da shi ' Ajiyar zuciya tayi shirin da suka haɗa ita da Samy baby yana mata yawo a zuci , sannan makirar zuciyar ta na cigaba da mata huɗhuba tace " ina nufin tunda Yarinyar nan kowa dai ya riga yasan irin rayuwar da take yi kafin a laƙaba maka auren ta dan haka na ga gara ka dawo da ita nan kana lura da ita dan saboda kar ta cigaba da yin ''yan harkokin ta tunda dai mai hali bai fasawa daga haka kuma ta kwaso mana ƙajaga ta shafa mana ko kuwa a maƙalo  baragurbin ƙwai a liƙa maka ya ƙyanƙyashe ya zamar mana bala'i a doron ƙasa ko me ka gani Doctor na ? Shiru ta ji bayan gama bayanin ta , sai ta ɗago kanta a hankali ta ɗaura ganin ta kan fuskar sa . Yanayin da ta hango akan fuskar sa ya tsinka mata zuciya ta ɗan yi yaƙe sanan ta ce "Docto.... Da hannu ya dakatar da ita wani irin murmushi yake da ya mata wuyar fassara yace , " Sofi kin yi tunani mai kyau , wanda na riga ki yin makamancin sa . . Ya ɗan yi shiru yana kallon yadda faffaɗan murmushi ya cinye fiye da rabin fuskar ta , ya cigaba da cewa " Fitar da nayi a ɗazu gidan da tayi rayuwa tsawon shekarun da tayi bata gida nan naje , kuma Alhamdulillah Amina ta samu shaida saɓanin wanda ni da ke da wasu tsirarun mutane wataƙila ka iya hasashe , Amina ba rayuwar banza tayi ba , asalima yaudarar ta aka yi aka taho da ita Abuja . " babu wata hujja ɗaya da zata sa a cigaba da yi mata kallon wacce tayi yawon banza, da ya wuce mummunar ƙaddarar da ta faɗa mata da kuma Allah ya iyakance mata shi , dan haka ina so daga yau ke ma ki cire wannan zargin daga ran ki Wafaa nitsattsiyar mace ce wacce ta tafi neman ilmi kuma ta samu dai-dai gwargwado da fatan kin gane ? Ya ƙarasa zancen yana kallon cikin idanun ta da suka yi wani irin mitsi-mitsi tana kallon sa , bai jira amsar ta ba ya cigaba da cewa "Amma duk da haka na karɓi shawarar da kika kawo na dawo da ita kusa da mu dan haka ina ga ranar juma'ah zan tafi Maidugurin sai kawai mu zo tare amma ba a ɗakin 'yan aiki zata zauna ba ɗakin 'yan aiki na 'yan aiki ne ita kuma Mata ta ce dan haka zata zauna a ɗakina kafin na samu gida nan kusa da ..... Zuruf! Sofi ta miƙe daga kan ƙafafun sa jikinta har mazari yake ta fara cewa. " wallahi Hamza baka isa ba , baka isa ka mayar da ni wata wacce bata san kanta ba , dan ka je an faɗa maka ƙarya da gaskiya shine zaka hau kai ka zauna ba bincike ba kome ni nan na san har gidan da tayi rayuwa a ciki tana sheƙe ayar ta a 'yan iskan samarin garin Abuja kaf ɗaya-ɗaya ne basu kwana da ita ba dan haka wallahi ba zan yadda ina zaman-zamana a kwaso min ciwo a yarɓa min ba sai dai ka zaɓa wallahi ko ni ko ita . Da sauri ta juya har tana tuntuɓe kome yana shirin kwaɓe mata dole ta yi yunƙurin ɗaukar mataki mafi tsauri da zai kawo mata ƙarshen kome **** Mutanen Maraɗi sun juya tare da Falmata da Hajja a ƙarƙaahin rakiyar Amnee da zainab  wadanda kwana biyu kawai zasu yi su wuce Chad Amnee zata je yiwa dangin su na can gaisuwar bangajiyar biki tare da godiyar hidindimun da suka yi musu.. Sun samu tarɓa mai kyau daya shafi wajen kwana tare da cimaka masu kyau da kuma tarin girmamawa daga bayu da hadiman gidan sarauta. Daga Hajiya Umma kuwa babu yabo ba fallasa tun zuwan su sau uku kaɗai ta zauna da su waje ɗaya. Ranar farkon zuwan su da kuma washegarin zuwan su da suka je gaishe da Maimartaba sai kuma yau da suke yi mata Bankwana nan ma kadaran-kadahan suka gaisa Amnee ta ɗanka mata amanar Falmata , tana sake jaddawa akan a yi kiwon ta saboda yarintar ta kada a bar ta da kankin kanta . Amsar da Hajiya Umma ta bayar ya sanyayawa Amnee jiki domin kuwa cewa tayi " Ɗa ai na kouwa ne itta kouwa ɗabi'a ta mai itta ce hali kuma shi ke samar da gurbi . " Babu Shakka. Amnee ta amsa mata . Tafiyar su ta karya zuciyar Falmata yadda bata zata ba , ta dunga kuka tana hangowa kanta rayuwar da zata yi a cikin wannan makeken gidan alhalin shi wanda take zaune domin sa bai ma san da zuwan nata ba. Tun bayan tafiyar su sai Falmata ta zama shiru koyaushe tana cikin babban ɗakin da aka mallaka musu ita da Hajja , wanda yake cikin falo na farko a shiyar , abunda ke fitar da ita gaishe da Hajiya Umma da suke zuwa yi kullum safe ita da Hajja daga sun dawo bata kuma fita sai kuma wata safiyar , Bayi biyu da aka ware mata su ke hidimar abincin ta tare da kula da tsaftar ɗakin da take , babu abunda take daga zama sai kwanciya , baki ɗayan rayuwar bata mata daɗi ga zaton ta idan sun iso zata samu ko da damar da zata dunga yin waya da Biyamuradi Youssouf sai ta tarar da rayuwar masarautar ba yadda ta saba ba , kowa a cikin gidan bisa umarnin na sama da shi yake aiwatar da lamura . Duk yadda Siyama da Aicha suka so su dunga jaan ta fira zuwa falo taƙi yarda ,dan haka suka ƙyale ta lokaci-lokaci Siyama kan shiga ɗakin su gaisa sannan su ɗan taɓa hira saboda gidan sarauta suke kome kake idanu na kan ka zai iya zama abun magana ko ma gorantawa ace kullum ita ke zaryar shiga wajen Falmata a matsayin ta na kishiyar ta . ita kuwa Aicha daman bata cika zaman gidan ba saboda tana shirin kammala karatun ta , dan haka Falmata kaɗaici ya mata yawa . har gara Hajja da daman ita bata ɗau zaman ɗakin ba ficewar ta take can shiyar Bayin gidan su sha hirar su duk da cewa ba wai aiki take yi ba . Yau tun safe ta tashi da ciwon baya da ƙafafu saboda cikin kwanaki biyun abunda ke cikin ya fara mata nawi ga yawan motsi da yake yi dan haka sai ta gagara ko da zuwa gaishe da Hajiya Umma kamar yadda ta saba tayi kwance lamo tana jin yadda abunda ke cikin ta ya cure gefe ɗaya. Hajja ita ɗaya ta tafi gaishe da Hajiya Umma ita ma ba wani sakar mata fuska Gimbiyar take yi ba "ah to Hajiya Umma ce fa ɗiyar Saraki matar Sarki ? Hajja ta so ta sanar da Hajiya Umma rashin jin daɗin da Falmata take fama da shi a yau sai dai yadda tayi wofintar da ita ya sa ta gaza shigar da batun Falmatan, ta ga sai umarni take bayarwa ga bayu ga Alama dai wani shiri na musamman ake yi yau a gidan . Dan haka sai Hajja ta miƙe jiki a sanyaye ƙasa-ƙasa tace "bana iya ba wannan gurfanon ya na me neman gafara ni ba lafiyar ƙafa na cika ba , a ƙare ƙalau wannan bautar mai ciwo ? ai ni ba sayo ni aka yi ba dan haka ba baiwa bace da za'a isheni da wani ƙaburi, duk na gundura da zaman gidan nan  Babban Soja Allah ya baka lafiya mu samu mu koma gidan mu inda muke a sake ba wata takura . Bata koma ɗakin ba sai ta fita can inda ta saba hira cikin bayu amma yau sai bata same su sun yi sansanin hira ba kamar yadda suka saba , sai shiga da fita kowaccen su take yi akan aiyukan su hankalin su bai kan ta. Ɗan zaman mintoci tayi ta miƙe domin komawa ciki kan hanyar ta suka ci karo da Babbar baiwar da take kula da shiyar abincin gidan wanda a shekaru aƙalla zasu yi sa'o'in juna bayan sun gaisa har Hajja ta gota sai Tabawa ta dawo da baya tayi ƙasa-ƙasa da murya tana ɗan leƙen baya tace " Hajja Hauwa da fatan dai kin taya Uwargiyar ki shiri ? Dan Kin kouwa san ɗiyan yanzu ba irin mu bane masu duƙufawa bauta ga Miji . A ɗan jahilce Hajja tace "Shirin me fa Tabawa ? Kama haɓa tabawa tayi tana ɗan karkata kai tace "kada dai kice min Uwargijar ki Gimbiya batta da sanin Yarima na daf da shigowa Masarauta ba ? dan kouwa a halin yanzu ma suna Niamey zuwa yammaci kouwa suke shigowa nan . Da hannu biyu Hajja ta dafe ƙirji muryar ta na bayyana mamakin ta tace  " Dan Allah fa Tabawa? A mamakance ta cigaba da cewa "yo ina kuwa muka sani muna zaune bonono , ai tsayuwa bata ganni ba dole na yi hanzarin komawa ciki, ke dai tabawa nagode miki. A zaune ta tarar da Falmata tana mammatsa yatsun ƙafafun ta da suke mata tsiko , ba tare da ta ɗago kai ba ta amsa Sallamar Hajja wacce ita ma kai tsaye ta zarce banɗaki ,bata tsaya yi mata dogon bayani ba  . ruwa mai zafi ta tarawa Falmata ta tuttula duk turarurrukan wanka da ta tarar da su a guri na musamman a jere da wasu ma ƙila ba na wanka bane ita dai Hajja ta zuba ƙamshi gum kuma ya cika banɗakin ya ratsa har waje . "Fatima tashi ki je kiyi wanka maza-maza zama bai gan ki ba 'yar nan . Hajja tace haka lokacin da take dawowa cikin ɗakin Falmata da ta riga ta saba da subaɗaɗin Hajja ta ɗan dubi Hajjan tana komawa ta kishingiɗa a ƙasa tace "Hajja duk yaushe nayi wanka da safe ? Sannan kuma wanka da tsakar ranan nan ƙarfe ɗaya saura Hajja lafiya dai ko ? " lafiya lau sai Alheri 'yar nan domin kuwa yau Ubanɗakina ke dawowa Babban soja Baban Mama yau amaryar ki kike uwarɗakina wankan taryar miji za kiyi . "Da gaske Hajja ? . Falmata ta tambayeta tana miƙewa  zaune fuskar ta ɗauke da yanayin da tashi ɗaya ba'a ba shi matsayi ba . bata jira Hajja ta bata amsa ba ta cigaba da cewa " Amma kuma ba wanda ya faɗa mana ko Maman Yumna ma bata faɗa min ba anya Hajja da gaske ne ? wa ya faɗa miki ? . " mts , ahaf ai ga irinta nan ke wa ya faɗa miki kishiya tana zama abar dogaro ɗari cikin ɗari ? Wa yace miki ana bada amanna da Amana baki ɗaya ga kishiya ? Ni daman daga ganin yadda take miki nan-nan nasan tsagoron kissa ce da kilbasa ai kin ga ga shi da tasamu labarin dawowar mijin ku ɗif ta ɗauke ƙafa tana can ta duƙufa shirya kan ta , ta bar ki baki sake , "Yanzu kiyi maza ki tashi ki gyagiije dan waɗannan ƙananun muri-mirin kowacce mai ciki sai tana yin su basu isa hana kome ba ai ciki ba cuta bace , kiyi azamar yin wankan ki fesa ado irin na shiga gasa ki tafi gaida Mahaifiyar sa daga nan ki zauna a falon ciki wajen ta , ta yadda daga ya sanyo kai falon zai gan ki tunda kuwa dai daga ya iso gidan gaishe da ita shine abu na biyu da zai yi bayan gaishe da Mahaifinsa , kin ga ita Siyamar take ko wa ? Da take miki ƙafar ungulu kin riga ta ganin sa , tashi maza uwarɗakina ba'a bori da sanyin jiki ... "Hajja ni dan Allah ki rabu da ni , kina ganin dai yadda koyaushe muka je gaishe ta ɓata rai take yi dakyar take ansawa sannan ..... Kafin ta ƙarasa Hajja ta katse ta "banda abun ki uwarɗakina faɗan da ya fi ƙarfin ka ai mayar da shi wasa kake , idan ta amsa yau da kyar watarana da fara'a zata tare ku ke da 'yan jikokin ta kiyi haƙuri kin ji  inda ba'a son ka anan arziƙin ka yake ke dai gwada mata ɗa'a sai ki ribaceta da kyawawan ɗabi'u kin san su saraki ne sai ana musu bangirma kin jii ko?  . Turo baki Falmata tayi da cigaba da cewa "  sannan Hajja shi ma ɗin ai bai ma san mun zo ba tunda kin ga fa bai taɓa neman mu ba gaskiya ni ba zan kai kaina wajen sa ba idan shi ya zo shikenan idan bai zo ba ma ni..... Wannan karon a hasale Hajja tace "to ai shikenan zauna kiyi ta jiran sa anan shi da yayi yi jinyar ya zo ya gaishe ki Iya-gwamma , tunda ni dai ba ki ɗaukeni bakin kome ba a zaman mu ban isa baki shawara ba ai shikenan . Daga haka tayi ficewar ta Bayan fitar Hajja a ɗakin sai duk jikinta yayi sanyi , tunda take da Hajja bata taɓa ganin tayi fushi ya haka ba duk sai ta ji ba daɗi dan haka ta miƙe a hankali ta shiga banɗakin Bayan fitowar ta da daga banɗakin da ta kwashi wajen mintoci talatin a ciki tana wanka. jikinta ba kuzari ta zauna a kujerar gaban gadon , har yanzu Hajja bata shigo ɗakin ba , tunanin da yake nuƙurƙusar ta sake yawaita yake yi "da gaske yau yake dawowa amma bai neme ta ba ? Tun rabuwar su har yau bai taɓa jin kewar ta ba kenan ? Shiyasa bai neme ta ba , tunda Aicha tace suna yin magana a waya kuma ko bayan dawowar su maradi rannan da kunnen ta taji suna waya da Aicha , kenan ita ce bai nema saboda baya buƙatar ta ko me ?  to meyasa ita kuwa zata damu kan ta da tunanin sa ? Har Hajja zata matsa tayi wani shiri na musamman a domin taryar sa . Har ruwan jikinta ya bushe bata shafa Mai ba , agogon ɗakin ta duba ƙarfe biyu har da kusan rabi dan haka ta miƙe ta sake komawa banɗakin tayi Alwala ta zo tayi Sallar azahar bayan ta idar bata miƙe akan sallayar ba ta cigaba da zama akai tana istigfar lokaci-lokaci tana murza idanun ta da suke mata mil-mil tunda tayi wanka da alama sabulan da tayi amfani da su wajen wankan sunfi ƙarfin lafiyar idanun ta . Tana zaune har aka ƙira la'asar bata jinkirta ba tayi Sallar kawo lokacin rashin jin motsin Hajja ya fara damun ta dan haka ta miƙe ta buɗe Babbar wardrobe bango guda da aka zube mata suturunta ciki ta dauko wata doguwar baƙar riga ta sanya a jikin ta ba tare da ta shafa ko hoda ba sai ɗan mai da ta mutsiƙa a fatar ta . Dawowa gaban Babban mudubin tayi ta tsaya tana duban kan ta cikin ta da ya ɗan tasa ya bayyana a sarari ta cikin rigar ta tsirawa ido. "Kunyar fita a haka ana gane mata cikin ya kamata ta . "Mts shi cikin nan ma duk ya bi ya hana mutum sakewa . tayi mitar haka lokacin da take cire rigar jikin ta ta zaro wata doguwar riga har lau launin ruwan zuma mai duhu da ya ɗan sirka da zane a tsai-tsaye launin farar ƙasa , rigar faffaɗa ce da take da rufaffen wuya sannan tana da ɗan nawi kaɗan a can Rochester ta taho da ita , lokacin da ta Sanya a jikinta ita da kan ta sai da ta ɗan murmusa saboda yadda rigar ta amshi zubin jikinta na dirarriyar mace mai matsakaicin tsawo da 'yar ƙiba kaɗan sai cikin nata ya ɓuya a rigar Rigar bata da mayafi dan haka ta ɗau wani babban mayafi launin farar ƙasa da aka masa adon duwatsu ta yafa akan ta ya rufe mata jiki kirif , har zata matsa daga gaban mudubin idanun ta suka kai kan 'yan kunnayen ta da tunda ta taho da su daga Maiduguri ta cire su ta ajiye ana,  su ta kai hannu ta ɗauka 'yan gajeru ne ta maƙala su a kunnuwan ta a hankali ta sanya ɗan yatsa ta lakaci mai ta shafe siraran labbanta marasa tudu . Takalmanta masu kama da silifa 'yan madina amma wannan daga Rochaster ta zo da su su ta zira a ƙafar ta ta fito bayan ta shafe jikinta da Humra da kamshin ta ke tashi kaɗan-kaɗan . Boyayyar ajiyar zuciya tayi lokacin da ta fito falon ta ga Hajja zaune daga gefe da alama Salla ta idar . Da fara'ar jin daɗin ganin ta ta matsa kusa da ita kafin tace " Hajjata anan kike ? Ɗan waigowa Hajja tayi kamar bata san da fitowar ta ba tace " uhm anan nake . " to sannu da hutawa Hajja nima yanzu na gama shirin zan shiga na gaishe su yadda kika ce . . Wannan karon Hajja ta ɗan saki fuska jin Falmatan tace zata yi yadda ta sa ta dan haka ta ce " to Madalla ko kefe fa uwarɗakina ? Maza je ciki ki zauna idan son samu ne ma ki samu wajen da yake fuskantar ƙofar shigowa ki zauna kin ji ko ? . " to Hajja Falmata ta amsa cikin ran ta tana gujewa rigimar Hajja ne amma idan ba haka ba ita ba wani niyyar zama tayi ba . Da kallo Hajja ta bi bayan ta cikin ran ta kakkabin wannan rigar ta Falmata take yi taɓe baki tayi kafin a fili tace " ana yi yafi ba'a yi tsarkin mahaukaciya da kunu , idan ba haka ba wannan riga da kika sako ai bata da maraba da buhu . A ɗarare Falmata tayi sallama a bakin  falon da daga inda take tana jin tashin hayaniya da dararrakin mutane da alama akwai wasu baƙi masu ɗan yawa a ciki . Ɗan jim tayi jin babu wanda ya amsa mata duk kuwa da tasan ana jin ta,  sake sallamar tayi a karo na uku sannan ta tsinkayo muryar wata daga ciki ta amsa , dan haka ta sanya ƙafafun ta ciki a hankali  . Da ɗai-ɗaya suke mayar da hankalin su kan ta tana tahowa har ta ƙarasa daga gefe kaɗan tayi ɗan gurfano tana gaishe da Hajiya Umma wacce tunda ta shigo ta rage fara'ar da take yi , kamar yadda ta saba amsa mata gaisuwar ba wata kulawa haka yanzun ma ta amsa tana janye ganin ta daga kan ta zuwa gefe kafin ta yunƙura  tana barin wajen baki ɗaya zuwa wata ƙofa daban . A hankali ta waiga tana ɗan kallon sauran matan da suke wajen biyu daga cikin su kawai ta gane "Ubbo da Ammi sauran mata ukun bata gane su ba amma dai suna mata yanayi da su Ubbo , cikin nutsuwa ta gaishe su a kunnen ta Ammi ce kaɗai ta amsa da mutunci sauran matan sama-sama suka amsa ita kuwa Ubbo ko amsawar ma bata yi ba . Fitowar Siyama daga ɗakin Umma yasa ta ɗago kan ta " sœurs wannan fa ? Kamar ya fi zama a jikina kou ? Ta ƙarasa zancen tana ɗan yin juyi cikin dakakiyar Shadda "Boo" da ta sha aiki aka mata ɗinkin doguwar riga , nan take wajen ya ɗau ƙaramar sowa suna yaba kyaun da tayi . cike da burgewa Falmata take kallon ta tana murmushi sosai ta yi mata kyau kwalliyar ta kuma ta ƙayatar da ita . " kin yi kyau Maman Yumna , muryar Falmata ta ratsa wajen . Da sauri Siyama ta waiga inda ta ji tashin muryar ta da farkon fitowar ta wajen bata lura da wanzuwar ta ba . Tana murmushi ta ƙarasa kusan ta kafin tace " Fatima nagoude sosai, yaushe kika shigo ? "Yanzu na zo . Ta amsa mata a taƙaice Murmushi tayi kafin ta ɗan yi ƙasa da murya yadda Falmatan ce kaɗai zata iya ji tace " Yau Yarima Biyamuradi ke dawowa , da fatan kin masa shiri ? Da yanayin ta na rashin magana sosai falmata ta girgiza kan ta kawai tana janye ganin ta daga kan Siyama ta sunkui da kan ta ƙasa duk jin ta take a takure sakamakon  kallon ƙasƙancin da ta lura matan wajen na jifan ta da shi . Muryar Ubbo ta ratso wajen da take cewa " Siyama kiyi maza ki shirya mana kin tsaya inda bai dace ba , kin san fa Mijin ki na daf da shigowa , kin kuma san ke tauraruwa ce  ba tururuwa ba , ke tauraruwa mai hasken alkhairi ce ba tauraruwa mai wutsiya ba . Cikin sanyin jiki Siyama ta juya fuskar ta ɗauke da yalwatatcen murmushin jin ɗadin yabo mai kama da ƙirari da Ubbo tayi mata sai dai gefe guda tana jin wani iri da shaguɓen da ta lura Ubbo ta yiwa kishiyoyin ta . Har tayi taku biyu ta waigo Falmata wacce kanta ke sunkui har lokacin ba tare da ta iya haƙaƙe halin da take ciki ba , ta saita muryar ta sama kaɗan kafin tace " Fatima taho mu tai ki sauya kaya akwai Boo irin ta jikina da tai min yawa nasan zata iya miki dai-dai tunda kin fini ƙiba kuma launin zai amshe ki'... " ahir ɗin ki da arawa kishiya sutura solobiya hala ita batta da sutura ta ratayo wagga tsumma a jikin ta ta taho muna nan tana barin mouna tsamin gwanjo ? . " ko da shike ba laifin ta ba nan gurin ta ƙurewa kenan , talaka daman yaushe yunwar ciki nashi ya lafa bare ya san suturar da ta amsa sunan sutura ? Bar ta cikin tsummokaran ta da shi yafi dacewa da itta .. "s'il te plait Adda amm Dan Allah . Da yanayi na rashin jin daɗi tare da chakuɗuwar tausayi Siyama ta juya ga Falmata lokacin da take mikewa tsaye ,  tayi saurin riƙo hannun ta tana cewa " kiyi haƙuri ƙamnata mu tai na miki le maquillage ki sauya kayan kin ji kou ? Idanun ta cike da ƙwalla wannan karon cikin wani irin yanayi ta zame hannun ta daga riƙon da siyama ta mata , tana ƙoƙorin danne hawayen da suke neman ɓallowa tace " Nagode Maman Yumna sannan ba sai na sauya kayana ba na jikina ma masu tsarki ne kuma kyauta ce daga Mijina masoyina ,dan shi na saka dan ya gani yaji daɗi ba domin na zama tauraruwa ba ina so ya ganni da su rataye a jikina dan yasan cewa na yaba da kyautar sa . Dan murmushi tayi kaɗan tana mayar da gani. ta kan su Ubbo daga inda take tana hango ɓacin rai akan fuskokin su da take iya gani dusu-dusu . " Nagode sosai Maman Yumna , ta sake faɗin haka lokacin da take barin wajen . Dusu-dusu take ganin hanya saboda idanunta da suke cike taf da ƙwalla ga kuma zogin da suke mata. bata tarar da Hajja inda ta bar ta ba , tana zaton tana ɗakin su a yadda zuciyar ta take yanzu so take ta samu waje ta ɓuya tayi kuka , ciwo ke sasuƙar rarraunar zuciyar ta da daman tana kusa jiran kiris take . Dan haka a karon farko tun zuwan su gidan ta fito ta ɗau hanya ba tare da tasan takamai-mai ina ta nufa ba bata kuma damu da bayun da suke binta da kallo har  wasun su na yin ƙus-ƙus ba so take tayi nesa da mutane ta samu maɓoyar yin kukan ta masha'in ' Can wani sashin da ta lura da ɗaukewar ƙafa ta shiyar nan ta nufa ,lokacin da ta doshi mashigar sashin tun kafin ta ƙaraso masu gadi biyu suka dakatar da ita , tambayar ta suka yi wacece ita ? Ta basu amsa da ita ce Fatima , suka ce daga ina take ? Tace daga Maiduguri Nigeria . Juyawa suka yi gefe suna ƙus-ƙus Cike da gundura ta juya da nufin fasa shiga ta nemi wani wajen saboda gaba ɗaya cikin gidan ne bata son komawa sai ta tsinkayo ɗaya daga cikin bayun yace " Ranki shi daɗe uwargijiyar mu afouwa muke biɗa ki maouna sassauci rashin sani ya sanya mu turjiya ga oumarnin ki baa in miki jagora ƙofa a buɗe take ga Iyalan Yarima Biyamuradi.. Sai suka buɗe mata ƙofar gidan daga inda take tana iya hango ƙawatuwar harabar gidan da shukoki masu furanni da bata ga irin su ba a kan hanyar ta ta zuwa nan , dan haka sai ta sanya ƙafar ta a hankali cikin harabar gidan ƙamshin furanni tare da na sabon fenti da wankin da aka yiwa gidan ya sanya ta lumshe ido ta fara taku tana jin yadda sanyin wajen yake ratsa ta shirun wajen yana samar mata da wata nutsuwa ta musamman sai kawai ta miƙa hanya ba tare da tasan inda zata je ba . Bakin wasu manyan gine-gine uku ta bullo tana ƙare musu kallo gini ne mai matuƙar kyau da tsari , ta tafi a hankali kan barandar ginin da yake fuskantar ta a tsakiya ta zauna daga bakin barandar ba tare da ta damu da shirun da ya yawaita a wajen ba bare ta ji tsoro sai kunnuwan ta da suke tarwai tana jin sauƙar kukan tsintsaye . Tana zama ta ji ƙuntatciyar zuciyar ta ta fara warwarewa lokacin da kuka mai ƙarfi ya zo mata , ta dunga tuno yadda baki ɗayan 'yan uwan Youssouf basu son ta ciki har da Mahaifiyar sa kan ta . Sannan shi ɗin ma da ake kome domin sa bai damu da ita ba a halin yanzu ma bata san matsayin ta ba a wajen sa . A hankali ta kai rigar jikinta hancin ta ta shinshina lokacin da take tuno da kalaman Ubbo da tace duk ta cika musu waje da warin gwanjo , ita bata ji warin da rigar take yi ba sai ma ƙamshi irin na tsadaddun kayan da aka sayo su daga manyan shagunan da suka amsa sunan su da ya chakuɗu da ƙamshin humrar ta yake bada wani irin launin ƙamshi mai sanya shauƙi' Ajiyar zuciya ta sauƙe cikin ran ta tana tambayar kan ta ko sai yaushe ne su zasu huta daga gorin mutanen duniya ? Sai yaushe ne za'a fara musu kallon mutuntawa ? Hawayen ta ta shafe da hannun ta tana jin damuwar ta tana raguwa da tayi kukan , daga gefe ta hango bakin fanfo ta yunƙura a hankali ta nufi wajen wanke fuskar ta tayi kuma ta tari ruwan da tafukan ta ta sha , ta kulle fanfon ta dawo ta zauna inda ta tashi . Wasu kyawawan duwatsu farare kal-kal ta gani daga gefe a ɗan gurin da aka killace domin yin shuke-shuke ta sa hannu a hankali ta tsinto su , ta zube su a gaban ta tana kallo cikin ran ta tana tunanin me ake yi da su kuma ? Jingina kanta tayi da jikin barandar tana rintse idanun ta saboda iskar wajen da take jin ta mata yawa kamar tana ƙara mata ciwon idon . Da ta rufe idon sai taji daɗi sannu kan hankali taji zaman ya fara mata ba daɗi saboda bayan ta da ya fara ƙagewa , bata damu da ta buɗe idanun ta ba da daman tafi sabawa da duhun dake cikin su. sai ta kishingiɗa kaɗan da nufin bawa kanta hutu na wani lokaci ,  sassanyar iskar wajen haɗi da shirun da wajen yake da shi da kuma yanayin jikin masu ciki yasa bata jima ba baccin da bata san yaushe ne ya kawo mata ziyara ba ya ɗauke ta a wajen . Lokacin da Biyamuradi Youssouf ya iso baki ɗayan Masarautar sai ta ɗauki murna da kiɗe-kiɗe tamkar wanda ake gagarumin biki . Da kyar ya samu ya zille daga fada nan ma domin uzurin da Tafeeda ya shigar ne na cewar da yayi ya kamata ya samu hutu tunda bai cika lafiya ba har yanzu . Da ya shigo gida sashin Hajiya Umma nan ɗin ma a cike ya tarar da sashin da katafainin 'yan uwansa waɗanda dai suke cikin ƙasar kama daga waɗanda suke ciki ɗaya har 'ya'yan Hajiya Mama da suke gidan tuni sun yi zangon a ɗakin mamar su labarin tabbatuwar shigowar sa yasa suka yi ɗango zuwa sashin Hajiya Umma. Haka ya dunga gaisawa da wasu wasu na rungume shi wasu har 'yar ƙwalla suke na jin dadin sake ganin sa a tsaye kyam bisa diga-digan sa irin taryar da suka masa ya sanya shi jin hawaye bai taɓa sanin haka yake zakara a cikin 'yan uwansa ba sai yau , babu shakka da mutuwa yayi da ya bar musu miƙin da bazai gogu ba a zuci . Daga can lungu ya hango Siyama ita ma ƙwallar farin-cikin ganin sa take tare da tasowar ciwon kewar sa da take yi , ɗan bakin nan nata yaƙi rufuwa daga murmushin da take kamar yadda ta kasa janye idanun ta daga kan sa. da hannu ya yafice ta yana 'yar dariya tare da jin raguwa ciwon da yake ji a cikin ran sa kan abunda ya same shi yana yin ƙasa da kusan kaso 50% ganin soyayyar 'yan uwan sa ya ishe shi farin-ciki . Tana murmushi ta ƙaraso zata tsugunna daga gefen sa ya sa hannu biyu ya ɗago ta ya matsa tare da yi mata wajen zama daga gefen sa da fara'a cikin sautin sa yace " Mata ai geufen Mijinta take da mazauni ƙaƙa za ki ɓuya bayan Aicha kina leƙe na ?  Ina ɗiyata ban ganta a masu tarɓa ta ba . " tana bacci'  ta bashi Amsa tana sake riƙe hannun sa da yasa cikin nata a lokacin ji take kaf duniya ba wanda ya kai ta jin farin-ciki har wani narkewa take jin zuciyar ta na neman yi bata ƙi ba kowa ya watse a bar su tare . Wajen ya ɗau dariya wasun su na tsokanar Siyama suna cewa kunyar kinibibi take yi bayan tun ɗazu ta ishe su da leƙe-leƙe . A cikin su duk babu wanda ya tado da batun abunda Maimounatou tayi masa da wannan kuma umarni ne daga Maimartaba da kan sa da yace " kada a maida zancen labarin tattauna akai . Hajiya umma ta miƙe tana barin wajen zuwa cikin ɗakin ta a lokacin Allah kaɗai yasan Halin da zuciyar ta ke ciki tayi rauni bata taɓa zaton zai dawo haka ras da shi da lafiyar sa ba babu shakka Allah shine mai yin yadda yaso da bawan sa wani ɗan Adam can bai isa tasiri ba. Bayan Miƙewar ta bai fi mintoci uku ba shima Youssouf ya mike cikin ran sa ya fahimci Mahaifiyar sa na son ganawa da shi dan haka ya bi bayan ta zuwa cikin ɗakin . Bayan yayi Sallama ya tura kai ciki , bisa sallaya ya hango ta riƙe da Alkur'ani  , ta ɗago kan ta tana saita ganin ta a kan shi fuskar ta ɗauke da Murmushi ya ƙaraso daf da ita ya zauna yana riƙo hannuwanta baki ɗayan raunin da yake ji a lokacin shine ya taso masa " Umma Allah shi min dawowa ban mutu ba kamar yadda suka so . .. ya furta hakan hawayen da suka cika idanun sa na sauƙa , yana jin yadda zuciyar sa ke yin kuka. a take ita ma zuciyar ya ta karye tun faruwar lamarin yau ne rana ta farko da Youssouf ɗin yace wani abu yau ne kuma rana ta farko da ta ga kukan sa a tunda ya zama cikakken mutum. Kan shi ta ɗora hannun ta kafin tace " ka dawo Youssouf ita cuta ai ba mutuwa ba wani kuma bashi da tasirin datse rayuwar wani sai fa idan kwanaki sun ƙare ka yi godiya ga Ubangiji doumin shi ya baka kariyar da basu idda nufin su ba Allah ya sa hakan ya zama kankara na daga zunuban ka . " Amin-Amin Umma,  ya amsa yana goge ƙwallar sa da hannuwan ta duk biyu ta taya shi tamkar dai lokacin da yake ɗan yaron sa. " Kar ka yiwa maƙiya kuka kamar kai ba jarumi bane ? Hakan zai iya barantaka da matsayin da kake kai na Soja mazan Fama sannan kuma Yarima sarkin watarana jarumi bai yiwa maƙiya kuka idan sun kai shi ƙasa ya samu dama miƙewa yake ya gyagije a cigaba da fafatawa . " hakan ba kome bane da ya wuce ƙarin ilmi cikin zaman duniya ka lura ka gane ba kowanne so bane yake zama na gaskiya , ba kowanne murmushi bane yake zama na ƙauna wasun ai shiga suke irin ta burtu suyi aron halayya da kamanni domin cimma wata mummunar manufa tasu su idar da mugunta ka kiyaye Yossoufa . Kallon ta yake bai ko ƙifta idanun sa zuciyar dake ƙirjin sa ya buɗe yana ƙarbar duk wasu kalmomin ta yana musu adana saboda dayawa daga cikin zantukan ta  bai kai ga gane me take nufi ba a yanzu ? Har kawo yanzu cikin ruɗani yake mai yawa ' har kawo yanzu zuciyar sa bata bar nacin tambayar sa me yasa Maimounatou tayi masa haka ba ?  yana son ganin ta domin ita kaɗai take da amsar tambayar nan . Ga mammadou ya kasa amincewa kiyayyar da yake masa har ta kai ya kashe shi ? Mammadou ɗan uwan sa ne da yake kusa da shi a haihuwa cikin jerin 'ya'yan gidan mutane biyu ne kaɗai a tsakanin su Bilal da kouma Yacouba da suke ɗaki guda. Hajiya Mama kouwa da ɗai ba zai yafe mata ba da ta zama jagora na lalacewar rayuwar sa da zama tsanin faɗawar sa a duk wasu munanan aiyuka da yayi a baya. Muryar Hajiya Umma ta katse masa zurfin da yayi cikin tunani inda take miƙa masa 'yan mukullin ɗakunan sa tana cewa "Magarib ta gabato ka tai kayi haramar Sallah nasan Maimartaba zai nemi ganin ka doumin ku tattauna ya ji ra'ayin ka kan duk waɗanda suka maka ƙeta kada ka cutar da kan ka wajen hanawa a bi ma hakkin ka ,  ka yafewa wanda duk zuciyar ka ta amince da yi masa yafiya , kada kouma ka ɗaukarwa kanka aniyar zama da wanɗanda zuciyar ka bata aminta da su ba ka saukakewa kanka sake faɗawa ga hatsari irin wanda ka fito a baya Allah ya ƙara ƙiyaye mouna kai sannan ka tsanan ta addu'a . "Amin Umma na kouma gode sosai Allah ya ƙara nisan kwana tare da lafiya . Lokacin da ya fito mafi yawan 'yan uwansa  sun watse sun tafi hidindimun su wasu kuma suna haramar sallah Ubbo ce kaɗai a zaune da ya fito dariya suka yiwa juna shi da ita yana wucewa tace " Fita kake yi Yarima ? " zan tai Sallah , ya ce mata yana ƙarasa ficewa . Bayan ya idar da Sallah gajiya duk ta taso masa tun yana sallar yake hamma dan haka bai tsaya sauraran masu son gaisawa da shi ba ya nufi cikin gida sashin sa ya tasamma saboda so yake yayi wanka da ruwa mai ɗumi ya ɗan huta kafin lokacin isha'i da yasan bayan sallar isha zasu gana da Maimartaba . Masu gadin shiyar sa suka buɗe masa ƙofa ya shiga , haske ya wadaci harabar da taimakon security lights dan haka ya nufi sashin sa kai tsaye yana janye ganin sa daga shiyar da Maimounatou tayi zama da ƙoƙarin son raba zuciyar da damuwar da take rufto masa ya hau kan 'yar barandar sa ya kai hannu yana kunna wuta domin ya samu damar buɗe ƙofa . Zuciyar da tai masa wani ɗan ƙaramin tsalle lokacin da ya lura da wanzuwar mutum kwance akan barandar kusa da ƙafafun sa , "Wanene nan ? ya tambayi zuciyar sa yana yin baya kaɗan cike da mamaki yana kure kallo zuciyar sa a dake da ƙoƙarin ganin fuskar ta da ta juya baya tana baccin ta hankali kwance Motsin sa da yayi da ɗan ƙarfi yasa ta motsawa ta juya zuwa rigin-gine tana motsa idanun ta da suka yi nawi . Saƙare yayi yana duban ta karo na farko da ya ji ya yarda cewa akwai Mafarkin ido biyu domin shi yake yi a yanzu. . "Fatima-zahra ya ƙira sunan ta a can ƙasan maƙoshi bata amsa ba saboda baccin da yake son sake danne ta . Tsugunno yayi a hankali kamar mai tsoron kar ya taɓa ta ta ɓace ya kai yatsun sa biyu kan fuskar ta ya shafa . Da sauƙar hannun sa a fuskar ta ta buɗe idanun ta da suke luf-luf cike da rauni ta ɗora ganin ta akan fuskar sa da "Fatima-zahra est-ce vrai ? Ehm ? est-ce vrai ?  Ya furta hakan muryar na 'yar ƙyarma . Hannun sa da yake cigaba da mata yawa a fuska ta riƙe da nata hannun kafin ta fara yunƙurin tashi sai dai kwanciyar da tayi a kan floor ba tare da shimfiɗa ba yasa jikin ta yin ciwo musamman haƙarƙarin ta . Lura da yadda ta kasa tashi farar ɗaya yasa shi tallafar ta gaba ɗaya ya zaunar da ita lokacin da shima yake yin zaman dirshan a ƙasa ya jingina ta da jikin sa kamar wanda ya tuno sai ya ɗaura dukkanin hannuwan sa biyu akan tudun cikin ta yana shafawa da buɗaɗɗiyar muryar sa yace "Fatima ki min magana mana don Allah , kece kuwa ? Kewar sa mai girma da take ta faman yaƙa tsawon watannin da suka yi basa tare ita ce ta taso mata baki ɗaya a yanzu ta kassara duk wata juriyar ta sai ta juyo a hankali rana ta farko da ta ɗaro hannuwan ta a fuskar sa ta riƙe shi da sanyi murya tace " Baban Mama est-ce vrai ? Meyasa ka tafi ka barmu tsawon lokaci baka neme mu  ba ?  meyasa ? Ka sa min ciwo a zuciyata ta , kasa kullum ina ta kuka . ƙarasa zancen tana janye hannuwan ta daga fuskar sa hawayen ta suka fara sauƙa . Riƙo ta yayi lokacin da ya lura tana jaa baya daga kusan sa cike da tsoron kar ta sake tafiya ta bar shi ya shiga share mata hawayen ta yana cewa " ke kika bar ni Fatima kin manta ke kika tafi ba tare da izni na ba ,  baki ko min sallama ba kika bar ni ? Fatima ke ma bakya sona ko ? Kan ta ta mayar kirjin sa da ƙarfi tana jin farin-cikin sake ganin sa tana jin kamar an bata maganin wata cuta dake cinye mata nishaɗin ta , ta kewaye shi da hannuwan tana riƙe shi ƙam-ƙam . "Oshh , yace yana ɗan ɗaga ta daga jikin sa saboda raunin sa da ta fama . "Fatima ina da rauni a jiki , baki san nayi jinya ba kou ? Idanun ta suka yi rau-rau tana kallon a hankali ta motsa bakin ta tana faɗin "sannu , Da ido ya amsa mata da yasan ba lalle  ta gani ba da nishaɗi cikin muryar sa yace "Ya babyn mu ? Lafiyar shi lau kou ? Naga yayi girma , ya zama babba alhalin bana ganin sa . Bai jira ta ba shi amsa ba ya ɗaga ta suka miƙe tsaye yana ɗora faɗin " mu tai ciki ki bani labarin yadda kika zou nan kuma ki nuna min Baby na na gan shi sosai . Ƙin motsawa tayi a hankali ta zare hannun ta daga cikin nashi kafin tace " nan ba shine masauƙin mu ba a can wajen Umma muka sauƙa can zan koma . Sake riƙo hannun ta yayi ya ja ta jikin sa ɗan tunbin ta ya tokare haɗuwar fuskokin su muryar sa a ƙasa da wani irin yanayi yace "to ai nan ne gidan ki nan da muke tsaye nan ne shiyar gidana nan shine ɗakina ya mata nuni da ƙofar ɗakin su . Cike da son samun haɗin kan ta ya cigaba da cewa ko kin koma yanzu tunda na dawo gobe nan za'a kawo ki , kin ga nayi rashin lafiya ma baki ko min ya jiki ba , muje ciki na nuna miki inda aka min fiɗa . Da sauri ta ɗago kan ta muryar ta tana rawa tace "yanka ka aka yi ? Aina ? Amma ka warke yanzu ? Ni fa ban san kana rashin lafiya ba sai da suka je tahowa da ni  suke faɗa . Langwaɓe kai yayi da son ta tausaya masa yace " nayi jinya iriyar wacce ban taɓa makamanciyar ta ba Allah shi ɗagga ni da war haka na daɗe a kushewata . Ta buɗe buɗe baki zata yi magana suka fara jiyo muryoyi ana hira da dararraki ana kusanto su , A tsorace Falmata ta zare jikinta daga nashi  a kunnuwan ta masu saurin ɗaukar sauti ta tsinkayo muryar Ubbo cikin masu maganar  , Muryar ta tana ɗan rawa tace " ni ni zan tafi ga mutane suna zuwa kar a ganni ace kuma na biyo ka . Yana ƙokarin sake riƙe ta taƙi yadda da sauri ta sauƙa daga barandar tayi bayan shuke-shuken da suke kusa da ita . Da wani irin yanayi yayi tsaye hannuwan sa biyu zube cikin aljihun wondon sa har Siyama da Ubbo suka ƙaraso wajen bayan su bayu ne su uku suna bin su ɗayar saɓe da Yumna a ƙafaɗar ta biyun suna riƙe da manyan tire-tire da aka jera abinci bisa . Kallon su yayi kafin ya ɗauke kai ya juya yana buɗe musu ɗakin "Biyamuradi daman kana ta tsayuwa nan ?  Ko kouwa yanzou kaima kake isowa ? Ubbo ta tambaye shi , Bayun da suke gaishe shi ya amsawa gaisuwar kafin su wuce ciki Siyama na gaba tana musu jagora. "Tun-tuni na zou Ubbo , ya amsa mata yana satar kallon inda Falmata take maƙale ran sa sam babu daɗi damuwar sa kar wani ƙwaro ya cije ta . " To ni zan koma sai da Safe ku kula da kan kou . Gyaɗa mata kai yayi lokacin da take juyawa Bayun da suka ajiye sakonni hannuwan su suna rufa mata baya bayan Siyama ta sallame su daga ciki . Suna ɗan bada tazara ya sauƙo daga kan barandar da sauri ya nufi inda Falmata take kafin ya ƙarasa daga bayan sa Siyama tace " Baban Yumna wani wurin kake tahia ?  Na haɗa ma abinci fa kouma ga wanka ma na tsumayen ka . Juyowa yayi yana kallon ta ya ga yadda ta ƙarya wuya tana tsare shi da idanun ta , a dai-dai lokacin ya rasa takamaimai amsar bata yana ganin ta ta taho har gaban sa tana murmushi ta saƙala hannun ta cikin na shi . "Ka bar koume zouwa gobe yanzou lokacin hutu ne Maimartaba da kan shi yace Umma ta sanar da kai ka huta yau sai daren gobe za ku gana . Jan hannun sa tayi tana 'yar dariya ta sake cewa "mu tai ciki na kula da kai Vous êtes mon patient pour aujourd'hui et je suis votre médecin.( kai marar lafiyan da zan kula da shi ne a daren yau nice likitar ka ) Cikin idanun ta ya mayar da duban sa yana lalubo fassarar kalmomin ta a cikin su,  murmushi ta sake yi masa tana kashe masa ido da yasa shi yin dariyar da bai shirya mata ba , cikin ran sa yana mamakin yaushe Siyama ta falle ya haka ? ya jaa ta jikin sa hannun sa riƙe da kugun ta suka juya tare muryar sa ƙasa-ƙasa yace mata " Fille, es-tu sûre que tu peux prendre bien soin de ça, ta patiente? ( Yarinya kin tabbatar za ki iya kula da wannan marar lafiyan naki da kyau ? Dariya ita ma ta saki tana rufe fuskar ta da tafukan hannun ta cike da jin kunya gefe guda zuciyar ta na madallah da 'yar uwa irin Ubbo da duk wasu shawarwarin ta basa wuce akan yadda zata yi ta karkato da hankalin mijin ta kan ta. Sun kai kan barandar sa ya juyo yana sake kallon inda Falmata take a idanun sa ya ga motsawar ta a wajen . Siyama ta jaa hannun sa zuwa ciki suka turo ƙofar . A hankali Falmata ta fito daga inda tayi maɓoya idanun ta shaɓe-shaɓe da ƙwalla zuwa yanzu ta tabbatar ita 'yar karo ce a wajen sa da kaddara ta haɗa su marar yanci ce ita da koyaushe take duƙunƙune a gefe. Siyama ita ce matar da take da 'yanci na yin duk yadda ta so da shi a lokacin da duk ta so amma ita ai a ɗosane take da kuskure kaɗan zata yi dangin sa su tunɓuke ta . Idanun ta suna ruwa ta baro sashin da kyar saboda bayan ta da yake rirriƙewa sai dai lokacin da ta tasamma komawa masaukin ta sai ta rasa hanya , Sai lokacin ta lura da sashi-sashi ne a ainahin gidan da duk gine-ginen su iri ɗaya ne sai ka lura da kyau zaka iya tantancewa ko kuwa idan daman ka san gidan sosai . A idanun ta da suke da rangwamen lafiya ga kuma duhun dare ba zata iya tantance ina ta fito ba sai dai tayi amfani da hagu da dama dan haka tayi hasashen sashin da yake hagu daga nan ta fito dan haka ta kama hanya . Ko a tsarin harabar sashin bata ga sauyi daga wanda ta gani a ɗazu ba shiru sashin yake babu kowa duk hadiman sun kammala aiyukan su sun tafi ga makwantan su . dan haka kan ta tsaye ta dunga ratsa falukan da ita take tura ƙofofin su da hannun ta har ta tarar da wanda ya mata iri ɗaya da nasu sai dai wannan ta lura kamar ba wancen ɗin bane saboda wannan babu kujeru sai wasu irin katifu da aka yiwa falon ƙawanya da su da ta tsaya da kyau ta lura sai ta ga kamar har labulayen falon ba irin waɗancan ɗin bane . Tana ƙoƙarin juyawa ta nemi wanda zata tambaya ko nan ne sashin Umma kamar yadda ta ji ana ƙiran surukar ta da wannan sunan , dogon kunnen ta ya fara jiyo mata tashin muryar wata mace daga ɗakin da tayi zaton masauƙin ta ne dan haka ta ɗan taka gaba kaɗan zuwa kusa sa ɗakin tana saurarar kalaman matar da take yin su cikin tashin hankali da hargagi . " Hafsatouwa ya zamo dole ki kouma wajen sa ki daɗa masa bayani da jaan kunne kada a samou watta matsala ga wannan karon wannan shegiyar ɗiya ta mutan agades da ta ɗora min jakar tsaba kaji sunka bini da tsattsaga ina buƙatar ya lalata min ƙwanyar ta , ta wanke ni ta wanke ɗiyana da bakin ta da ta min wannan sheri ta tona min asiri na da shike binne tsawon lokaci ina so ta lahe ɗoɗɗoyan aman da tayi da bakin ta . " shi kouwa wannan taƙadarin yaro ɗan tamri Youssoufa da ake kome bisa kan sa ina so a sabunta min aikin sa yayi tsamri fiye da na baya a ƙara hargitse shi a gigitar shi ya fice hankalin sa , itta hegiyar ɗiyar da ya amro dagga Nigeria a sanya shi i mata shika ukku russ tunda na lura shina ƙamnar ta sosai hakan zai ci ran sa ya zaburar sa komawa ga ruwa ina so ya zama tamre wurin bibiyar mata a baya ya kwana da ya ya auri ƙamna gaba 'ya da uwa nake fatan ya haɗa kada kouma ya saurarawa barasa ya zuƙe ta tamkar nonon uwatai ya zama lalattace irin lalatar da zata sa iyayen sa su yahe shi dagga cikin 'ya'ya mutanen gari su masa korar kare dagga birnin Maradi . "Daga nan na san baƙin-cikin haka shi zai kai Safiya ramin ta...tayi wata dariyar hango cikar buri . Daga ƙasan ta inda tayi gurfano Hansatuwa da take sauraron ta tana taya ta dariya tace " Ranki shi daɗe maganin kukana ai wannan kullin magani da na kawo miki shi ita uwar ta su anka ce ana so ta ci domin barin ta haka nan tsakani yana lalata mussu aiki kin san ta da ibadar ganin ido . " ar can kyale ta mu da muke ɗiyan liman ma munka saurarawa ibadar nan bare itta da haye tayi ɗaukar duman magaji da nishi dan kawai ace itta ta Allah , maganin ta nake yi wallashi sai na hana ta ga yin ibadar naga ƙaƙa ta ka yi ta lalata mouna aikin 'yar tselen uwa . "Hafsatouwa muddin aiki shi tafi dai-dai da tsarin mu ki tabbata shekarar gaba ke ai babbar jakadiyar birnin Maradi doumin kouwa waccen kaucewa take ta baki guri da hannuna zan sallame ta da wani mummunan sharri ta yadda zuri'ar ta basu yin gadon matsayin ta sannan ban tsaya nan ba cikin jama'ar ki ɗai-ɗaya ne ba za su Makka ɗakin Allah ba sai fa wanda Allah bai ƙira ba . Wata mitsi-tsiyar guɗa Ƙaramar jakadiya ta sake da hakan bai hana su jin motsin Falmata ba wacce a kokarin ta na yin baya ta ture 'yar randar da aka ajiye 'yar bishiyar fulawa daga sama kaɗan da inda take tsaye tana sauraron su tukunyar ta faɗo ta fashe . A tare suka zaburo ƙirjin su na dakan tara-tara da jin tsoron ko dai an musu laɓe ? "Idan kuwa hakane muddin ta kama mai mata laɓe sai ta sabauta shi kafin ta ɓadda shi ko wanene kouwa da dai ya fasa wannan sirri na ta mafi girma .Hajiya Mama ta aiyana hakan cikin ran ta lokacin da take nufar falon a ɗimauce . ASSALAMU ALAIKUM MASU KARATU DA FATAN KUNA LAFIYA TARE DA FATAN ALHERI . KUYI HAƘURIN JINA SHIRU DA KUKA YI UZURIN DA YA GITTA MIN MAI GIRM ne . A gaskiya bana jin daɗin ku masu karatu ta yadda bakwa musayan ra'ayoyin ku hakan ma na ɗaya daga cikin abunda ke duƙusar ni daga nayi yunƙurin yin typing sai nace "ah to yaya zan matsa kaina Alhalin ba'a nuna yabawa ?  Sai kawai na ajiye na fuskanci wani lamarin da ya zarta haka , da fatan kun fahimceni za kuma kuyi duba izuwa koke na ? Nagode ' [2/27, 9:35 PM] +234 706 503 6187: MAFARI (Hargitsin Rayuwa ) Umm'muaz 51 Da baya-baya Falmata ta fara taku tana jin wani tsoro-tsoro daga ƙasan ran ta kafin ta juya da hanzarin son gujewa haɗuwar su da ita da mamallakan muryoyin da ta ji suna kitsa sharri da bata kai ga sanin su waye ba . Sai dai taku biyu kawai tayi ta ji an fisgo rigar ta ta baya da matuƙar ƙarfi da ba domin rigar tana da faɗi ba da babu abunda zai hana ta yagewa bayan ta jefar da ita a ƙasa warwas . A tsorace ta juyo da taimakon hasken lantarki suka yiwa juna kallon tsakar ido tsakanin ta da Hajiya Mama , Ba tare da Hajiya Mama ta saki rigar Falmata ba tana ƙanƙantar da idanun ta da suke cike da tashin hankali tace "wacece ke ? Me kuma kike nema anan ? Wa ya aiko ki ? Sannan me kika ji ana cewa ? Falmata ta kif-kifta idanun ta da basu cika karfi ba kafin ta fara kici-kicin kwacewa cike da dakiya a muryar ta tace " Ni ce Falmata , matar unh ' Umh Yarima Youssouf Abdoul-aziz , kuma ki sake min riga ta na tafi . Wani irin zillo Hajiya Mama tayi a take gumi ya karyo mata ta shiga juya kan ta daga ɓangaren hagu zuwa dama baki ɗayan jikin ta tsuma yake . Idanun ta da suka fir-fito a halin yanzu su ta gwalalo cikin kufcewar nutsuwar ta ta shiga jijjiga Falmata da wata muryar da ta fi kama da raɗa take cewa "Annamimiya ke kuma salon ki kenan ? Da salon da kika zo kenan ?? Lalle kin yi kuskure mafi girma da da ɗai wallahi baki sake maimaita makamancin sa . Juyawa tayi tana jaan ta ita kuma tana turjewa , cikin ɗakin da suka fito ta koma jaye da ita tana shiga ta ingiza ta ba tare da ta kula da cikin jikin ta ba da sauran ƙiris ta faɗa kan cikin ba dan ta riƙe gadon da ta samu damar ƙarasawa gaban sa ba. Hafsatouwa da tuntuni bata samu damar cewa kome ba illa fargaba da ita ma ya cika mata ciki maƙil jin wacece Falmata , da matsayin ta a gidan da kuma alaƙa mai girma da take da shi da zancen da suke tsakiyar yin sa ita da uwargijiyar ta da babu shakka Falmata ta ji kome . Tana shiga ɗakin ta rufe ƙofar ta murza ɗan makulli da hanzari ta juya jin sautin mari da ya karaɗe ɗakin . Akan Falmata ta sauke ganin ta wacce ta durƙusa akan guiwar ta riƙe da ƙuncin ta da Hajiya Mama ta zage iya ƙarfi ta mare ta . Sake chakumota tayi ta ɗaga ta tana sake chukui-kuiye ta tace "za ki faɗa min me kika zo yi nan wajen a dai-dai wannan lokacin kuma wa ya turo ki ? me kuma kika ji ina cewa ? ko kuma sai na shaƙe ki kin mutu ? Falmata da zuwa lokacin hawaye ya gama wanke mata fuska zuciyar ta kuma ta cika da tsoro cikin rawar murya tace "wallahi ban zo yin kome ba kuma ba wanda ya aiko ni nan , mantuwa nayi na kasa gane hanyar komawa sashin da aka sauƙe mu saboda tunda muka zo ban taɓa fita ba kuma kin ga idona , idona wallahi bana gani mai kyau dan Allah kiyi haƙuri ku mayar dani sashin da Hajja take . "Ƙarya kike yi munafuka , me ya fito da ke a daren nan idan da gaske dindimin kike yi ? Baki bani amsa ba me kika ji muna tattaunawa nace ? Kuma uban waye yace ki min laɓe ? Mukut ! Falmata ta haɗiyi yawun tsoro cikin rashin sanin takamaimai amsar bayawar tayi shiru . Cikin rashin sanin ta shirun da tayi shi ya basu tabbacin ta ji kome , abunda suke gudun kuma yana gaf da faruwa watau fallasuwar asirin su . Falmata bata ankara ba taji sauƙar wani marin kafin tayi wani yunkuri ta ji sauƙar duka da dundu ta ko'ina kusan gabadaya Hajiya Mama bata hankalin ta dai duka kawai take kai mata . Ihun da Falmata ta buɗe maƙogoro ta rafsa shi yasa Hajiya Mama dakatawa daga dukan ta , idanun ta jawur ta juya ga Hafsatouwa tace "Hafsatouwa tai ki ɗauko min wuƙa mai kaifi ki kawo min . Da gudu Hafsatouwa ta miƙe daga durƙuson da tayi ta fita . Cak Kukan Falmata ya tsaya ta shiga wara idanun ta da ganin su ya sake yin ƙasa saboda kukan da take yi , ta fara taku tana laluben hanya so take tayi wani yunkurin tseratar da kan ta . Fizgota Hajiya Mama ta sake yi ta warɓar da ita a bakin gado da muryar da take cike da bushewar zuciya tace "ƙwarmato kike yi min ? Kina son tara min jama'a ? Yarinya baki sanni bane , amma za ki sanni dagga lokacin da na guntule miki halshe . Cikin neman agaji Falmata ta zube guiwar ta a ƙasa dai-dai da dawowar Hafsatouwa da take riƙe da wata sharɓeɓiyar wuƙar yanka dabba a cikin kuɓen ta hawaye na tsiyayo mata ta haɗa hannuwan ta biyu da sigar migiya tana cewa "Hajja dan Allah kiyi hakuri ki barni na tafi wallahi duk abunda naji ba zan faɗawa kowa ba , wallahi bazan faɗa ba , kiji tausayina ki ƙyale ni ko dan abunda ke cikina . "Ki min shiru hegiya , ina ruwana da hegen cikin ki ? Kar na kuma ji kin ƙira ni ba suna na Hajja ba . "faɗa min me kika ji ana cewa ? Maimaita min idan kuwa kika min ƙarya sai na yanka ki billahil azim. Tiryan-tiryan Falmata ta maimaita musu hirar su kamar yadda ta haddace akan ta ba kalma guda da ta manta duk a ƙoƙarin ta na son suyi mata afuwa bata tsaya da bayani ba sai da ta dire sannan ta ɗora da cewa "wallahi shikenan abunda naji kuma nayi Alƙawarin bazan faɗawa kowa ba . Sai dai tunanin ta ya tsaya chak lokacin da Hajiya Mama tayi wata gajerar dariyar da ke bayyana irin halin ɗimuwar da take ciki. "Bayan duk kin ji wannan sirrin nawa da mutane uku ne suka san shi bayan ni a din duniya ? Sirrin da 'ya'yan cikina ma basu san shi ba , sirrin da yake ginshiƙi na rayuwata baki ɗaya , da na ta'alaka duk wasu nasarorina akai , shine kike tunanin zan bar ki ki tafi ? Na barki ki tafi kiyi rayuwa a cikin gidan nan ɗauke da sirrina a hannun ki ? Ko a hankali irin naki na dabbobi hakan abu ne da zai yiwu ? Wata dariya ta sake yi kafin tace "yarinya wannan ba mai yiwuwa bane dole nayi abunda zai sa na kuɓutar da sirrina da yake hannun ki ... "Wallahi Hajja bazan faɗawa kowa ba . Falmata ta furta hakan tana sharar hawaye da rigar ta . "Ni da kaina zan goge shi daga kan ki ko da kuwa ace hakan ba zai samu ba sai na raba kan ki da gangar jikin ki ne ' "Hafsatouwa ban wuƙar nan . Da sauri ta miƙa mata ta sake komawa tana Sake jaan labulen windows din dakin. A hankali Falmata ta ɗago kai zuwa lokacin ta karaya cikin ran ta ta saddaƙar mutuwar ta ta kusanto , Idanun ta ta sauƙe akan Hajiya Mama , tana jin yadda zuciya da ƙwaƙwalwar ta ke adana hoton kamannin fuskarta , a matsayin matar da zata raba ran ta da gangar jikin ta . Fitsarin da take riƙewa ya kufce ya shiga bin ƙafafun ta lokacin da ta sauke ganin ta akan kakkaifar wuƙar da Hajiya Mama take jujjuyawa a hannun ta . Wani murmushin mugunta Hajiya Mama ta mata kafin tace "ke kina jina ? Cikin mutuwar jiki liƙis Falmata ta gyaɗa kan ta . "Kina da zaɓi biyu ko dai na yanka ki a yanzu na kar ki na kar banza , na sa a ɗau gawar ki a yasar , ko kuwa kiyi duk abunda nace da ke ba tare da gardama ba , sannan ba kuma na son na sake jin tashin sautin muryar ki, ko numfashi mai ƙarfi kika jaa sai na yanke miki hanci bare ta kai ki ga magana babu makawa za ki tsinci halshen ki a ƙasa kina jina ko ? Da sauri ta sake gyaɗa kai, wasu sabbin hawaye na sake tsiyayo mata . "Hafsatouwa ki je ki kawo min rigar bayu da mayafi . Kafin ta rufe baki Hafsatouwa ta yi waje , Nisawa Hajiya Mama tayi tana karkaɗa kafa cike da izza da mugunta tace "yarinya duk abun da kunnuwan ki suka jiye miki na kaddamar ina kuma kan gaɓar shirya wasu game da surukuwar ki da shi kan sa mijin ki haɗa da 'yal uwarki gasken gaske ne . "Ki kuma tabbatar zan iya yin abunda yafi haka akan ki muddin kika yi kuskuren yi mini gaddama ko da sau ɗaya ne . "Ɗauke idon ki daga kaina fitsararriya kin wani tsattsareni da ido uwa budurwar mujiya . Ta ƙarasa zancen da tsawa da hargagin da yasa abun da ke cikin Falmata murɗawa. Da sauri Falmata ta sunkuyar da kai tana jin tausayin kan ta na kawo mata , ita kuma irin tata kaddarar kenan mutuwa a hannun wannan azzalumar mata , da ita da abunda ke cikin ta , domin zuwa yanzu ta tabbatar babu wani mai tsaratar da ita sai fa Allah . Dawowar Hafsatouwa riƙe da wasu tsummokara yasa Falmata sake tsorata "ka dai toshe mata hanci za suyi su hanata mumfashi har ta mutu ? Saukar taunmokaran a jikin ta ya sa ta ɗago kan ta a firgice. "Ki tashi ki saka kayan nan da gaugawa . Babu yadda ta iya haka ta lafta waɗan nan kayan akan na jikin ta tana yi tana yunƙurin aman da yake taso mata sakamakon tsami da ɗoyin datti da kayan suke yi . "Kiyi lulluɓi da kyau ki biyo ni a baya muddin kika yi wata alamar da tasa aka gane akwai wani abu wallahi kafin ki farga na soke ki. Haka suka dunga ratsa sashi-sashi na gidan suna cin karo da bayu tsilla-tsillan da suke zubewa su gaishe da Hajiya Mama . Har suka dangana da wani sashin da yafi kama da kango da yake can ƙuryar gidan da daga shi sai maƙabartan da take cikin gidan ta ɓaryar dama . Da wani ɗan makulli Hajiya Mama tayi amfani ta buɗe ƙofar ainahin tangamemen falon da yake cikin sashin . Ta ingiza Falmata wacce bata kai ga sanin cewa falon ya shiga ƙasa ba dan haka tana jefa ƙafar ta ta faɗa ciki ta gurɗe a ƙafa kiris ya rage ta faɗa a kan cikin ta Allah ya sa ta tokare ƙasa da hannuwan ta . Lokacin da ta ɗago kai bata iya ganin fuskokin Hajiya Mama da Hafsatouwa saboda duhun da Falon yake ɗauke da shi , da raunanan idanun ta hasken da yake shigowa daga can harabar gidan yayi kaɗan su iya gani tare da shi . Ɗallare mata ido da hasken wayar hannun ta da Hajiya Mama tayi yasa ta saurin runtse idanun ta kafin ta buɗe su da sauri jin abunda Hajiya Mamar take cewa . " anan za ki cigaba da zama har zuwa lokacin da zan gama yanke hukunci kan matakin da zan ɗauka akan ki., idan kika yi yadda nake so ta hanyar zama salin-alin ba tare da kin yi wani motsin da zai sa asan kina nan ba , wataƙila na iya barin ki bayan na kafa miki sharɗaɗun cigaba da rayuwa a gidan nan . "Muddin kuwa kika yi yunƙurin yin wani motsi da zai sa asan kina nan wallahi , wallahi , wallahi , ni ina iya kashe ki da hannu na kuma na sa a ɓatar da gawar ki . Daga haka ta juya da sauri suka fita ita da Hafsatouwa daga inda Falmata take yashe tana iya jiyo saƙala ɗan makuba da aka yi aka kulle ta ta baya kafin ta fara jin sautin takun sawayen su akan busassun ganyayyakin bishiya su na barin wajen har dai zuwa lokacin da sautin su ya ɓace a kunnuwan ta . Wani irin karkawa tsokar jiki zuwa gundarin zuciyar su ka shiga yi na tsananin tsoro da firgicin da ruhin ta ke ciki , kafin da wani irin sauti ta fashe da kuka , ta shiga rarrafawa da hannunwan ta da guiwar ta zuwa inda take tunanin nan ƙofar take , Lokacin da tayi karo da bango da hannuwanta duk biyu ta shiga bugun bangon cikin ɗimuwar rashin fahimtar ƙofa ce a wajen ko kuwa jikin bango ? . Washegari da Asuba a Masallaci bayan sun idar da Sallah, Maimartaba tare da Youssoufa yana biye da shi a baya, kai tsaye sashin Maimartaba suka yiwa tsinke domin ganawa ta musamman . Maimartaba yana sake tambayar Sa yanayin lafiyar jikin sa ? Shi kuma yana amsa masa da cewa "yana cigaba da samun sauƙi sosai . Bayan sun isa turakar Maimartaba Youssoufa zai zauna daga gefen shimfiɗar da yake kai , yace masa "dawo nan kussa gareni mu tattauna yana masa nuni da kan shimfiɗa kusa da shi . Da jin daɗi mai yawa Youssouf ya matsa kusa da shi . Gyaran murya Maimartaba yayi kafin yace . "Youssoufa wanne mataki kake ɗauka bissa ga waɗan da suka ha'ince ka ? Shiru Youssouf yayi kafin yace "Ranka shi daɗe dukkanin hukuncin da ka zartar . Shiru mai martaba yayi kafin yace " Ubangiji Mai yawan yafiya ne , yana kuma ƙaunar bayin sa masu afouwa ga junan su a duk lokacin da aka zalunce su , shi yake tanada wa adalai taimako da kiyayewa, wato mutane masu aminci babu wani mugun abu da zai same su, amma mugaye ba za su sami kome ba, sai wahala bayan ubangiji ya bar su da kan su , Kada ka ɗaukar wa kanka fansa, ka dogara ga Ubangiji shi zai yi sakamako. Youssoufa da yayi shiru yana sauraron sa , jin ya dakata ya sa shi ɗago kan sa a nutse A kalaman maimartaba ya fahimci shawarar da ya ba shi cikin hikima ransa kuma ya sanyaya daga zafin da yake masa a duk lokacin da ya tuno da abunda aka masa dan haka sai yace "Nayi musu afouwa ranka shi daɗe amma ita ban iya sake riƙon Amren ta zan sauwaƙe mata daga can ta tai yankin su , mammadou kouma zan tafi mu dawo tare . "Madallah da kai Youssoufa yadda kayi afouwa ga 'yan Adam da sunka maka ƙeta kai ma Allah shi maka afouwa bisa tarin laifukan ka . "Amin Amin Baba . Murmushi maimartaba yayi yana jin ƙaunar ɗan sa na kawo masa tabbas zuciyar wasu sassauƙa ce mai yawan yafiya . "Yaushe za ka tafi Niamey domin kawo ƙarshen zaman su a magarƙama ? Ko kouwa saƙo za'a aika musu ? "Da kaina zan je doumin na sanya hannu a takardar da zai sa a sake su sannan ita kuma zan sahale mata amre na , cikin kwanaki biyu masu zuwa zan tafi . "Kafin tafiyar ka a sanya a tattara kayan ita wannan ɗiya a aika da su garin su , shiyar ta kouwa ni da kaina zan sa a shirya shi ga ita ɗiyar da muka amso amanar ta daga ƙasar su insha Allah ita tana cikin amintattun mu Allah ya cigaba da baku kariya baki ɗayan ku ya kuma dauwamar da zaman lafiya tare da zuri'a masu Albarka tsakanin ka da matayen ka . Wani irin farin-ciki Youssouf ya ji yana ratsa shi jin cewa ashe Maimartaba da kan sa ya sa aka dawo da Falmata har ma kuma ga shi zai sa a shirya mata wajen zama a gidan hakan yana nufin samun 'yanci tare da tabbacin zaman sa har abada da Fatima , idan hakane yana godiya ga Allah da duk wasu hatsararruka da ya tsallaƙe tunda ya tsira da Fatima-zahra. "Amin Nagode Nagode ranka shi daɗe Allah ya ƙara girma tare da nisan kwana . "Allah shine abun godiya Youssoufa . Sun jima suna tattaunawa Maimartaba yana ba shi shawarwari cikin hikima tare da yi masa nasiha har hantsi ya ɗaga lokacin zaman fada ya gabato , Tare suka yi karin kumallo kafin yayi bankwana da Maimartaba zuciyar sa cike taf da farin-ciki gami da nutsuwa ta musamman , tabbas wanda duk yayi dace da iyaye na ƙwarai ya samu rabi na daga nasarar rayuwar sa . Gefe guda yana sake jin haƙaƙewa akan rabuwa da Maimounatou bayan ta amsa masa tarin tambayoyin da kullum yake bitar su cikin ransa tare da burin jin amsa daga bakin ta . Bai koma sashin su ba sai ya zarce shiyar Hajiya Umma zuciyar sa cike da ɗokin son ganin Fuskar Falmata a hasken ranar da ta fara ɗagowa , yana da tabbacin a shiyar Hajiya Umma anan aka mata masauƙi . Abun Mamakin da ya tarar lokacin da ya riski falon Hajiya Umma bai wuce ganin ta tare da Hajiya Mama da sauran 'yan uwan sa baki ɗaya ciki har da 'yan ɗakin Hajiya Mama duk suna karin kumallo tare da hakan sosai yake sabon lamari a wajensu baki ɗaya . Cike da jin daɗin ganin su haka a tare ya ƙarasa falon kai tsaye kusa da Hajiya Umma ya zauna , yana gaishe ta kafin ya juya ya gaishe da Hajiya Mama wacce ta amsa cikin nuna tsantsar farin-ciki kafin ta ɗora da tambayar sa ƙarfin jikin sa ? A ƙarshe ta bi shi da wata doguwar addu'ar da yasa zuciyar Hajiya Umma haske har ma ta fara samun 'yar nutsuwa akan ta karo na farko , fuskar ta ta cika da annashuwa tana amsa jerin addu'o'in da Hajiya Mama ke yi . Da wata irin kulawa da ta zarce ƙa'ida Hajiya Mama tace "Yarima Magajin sarki me za ka ci a zuba maka ? Da jin ɗaɗin kulawar da take masa ya ɗan yi taƙaitatcen murmushi kafin ya bata tabbacin tare da Maimartaba suka yi karin kumallo . Wani murmushin yaƙe tayi ta jaa bakin ta tayi shiru sakamakon wata kibiyar baƙin-ciki da ta ji ta soki ran ta . Sallamar da Hajja ta rangaɗo daga bakin ƙofa bai sa wasun su sun tsagaita daga hirar da suke ba , sai fa Youssoufa da Hajiya Mama sune suka yi hanzarin amsa Sallamar da su biyun daman kunnuwan su tarwai yake ga sauraron mai iya shigowa a dai-dai lokacin . Daga inda Hajja ta saba tsugunnawa ta gaishe da Hajiya Umma yau ma daga nan tayi gurfano ta miƙa gaisuwar ta . Hirarrakin su suke cigaba da yi ba wanda ya kula gaisuwar Hajja bayan ita Hajiya Umma da ta amsa sama-sama sai fa Youssoufa da ya amsa a mutunce cikin girmamawa. Jim! Hajja tayi a zaune tana juya zancen da take tafe da shi a ran ta na rashin ganin Falmata ko sanin inda take a tun yammacin jiya . Wanda ba ƙaramin tashin hankali ya jefa ta ba , domin kuwa ko baccin ta rabi-da-rabi tayi duk kuwa da cewa wani ɓangare na zuciyar ta na shaida mata cewa Falmatan tana tare da Youssouf ne tsakanin Mata da Miji bare ma a haɗa dai da 'ya'yan zamani. Sai dai ganin Youssoufa a yanzu shi ɗaya ba tare da Falmatan ba ya sa taji cewa gara kawai ta tambaya domin samun tabbacin da zai bata nutsuwa dan haka ta gyara murya kafin tace "Ranka Ya dade Yarima ince dai Fatima ta kwana lafiya ? Domin kwana biyu tana fama da ciwon ƙafafu na saba mata tausa da asubar fari saboda ta ɗan ji dama-dama . A ɗan jahilce Youssouf yake kallon Hajja kafin yace "Hajja ina itta Fatima ta fita da safe hakka ita da bata cika lafiya ba ? Kalaman sa sun zo dai-dai da bugawar zuciyar Hajja a take ta ji wani tashin hankali mai girma yana durfafar ta cikin ruɗewa tace "ha'a ? Ai tun jiya bayan ta shigo nan domin taryar ka bata sake komawa ɗakin da aka mana masauƙi ba , ban sake ganin ta ba , yau Fatima bata kwana a ɗakin da aka sauƙe mu ba , ban kuma san inda take ba . Hajja ta ƙare zancen da baza hannuwan ta biyu cikin tashin hankali. "que de diable racontes-tu ? Youssouf ya furta hakan cikin ƙaraji tare da miƙewa akan ƙafafun sa da hakan ya jaa hankalin duk sauran mutanen dake wajen bayan Hajiya Mama da daman tuni take sauraron bayanan Hajja . Muryasa cikin tashin hankali ya cigaba da cewa "Hajja wanne zance ne wannan ? Ina Fatima ta kwana ? Tare da wa aka gan su sun fita ina kuma suka tafi ? Watsa hannuwa biyu Hajja ta kuma yi kafin tace "Allahu shi ya barwa kan sa sani ni dai ba shakka ban san inda ta tafi ba . Cikin nutsuwa Hajiya Umma da zuwa lokacin ta ji abunda Hajja take cewa ta dubi Youssouf "Mene ne ya faru ? Ta tambaye shi , wani ɗan taku ɗaya biyu yayi kafin yace "Fatima, elle est partie, elle est perdue. "comme quoi ? Ubbo ta furta hakan tana tsare Hajja da ido kafin ta ɗora da cewa "kuma sai dai idan da kan ta ta tai wani wuri . Hajiya Mama ta muskuɗa tare da cewa "wai meye ya faru ? Wace ce Fatima ? Damuwa na bayyana a fuskar Hajiya Umma tace "ɗiyar Nigeria da Youssoufa ke amre ita ce ta ba'a gan ta ba . Salatin da Hajiya Mama tayi ya sake dilmiyar da Hajja da Youssouf cikin ƙarin wata damuwar kafin tace "to ina ta tafi ? An kuma duba ko'ina ba'a gan ta ba ? Bai fa kamata a zauna ba a yi oumarni maza a fantsama neman ta cikin gida ba'a rasa inda tayi ba. Kafin a ɗau wani lokaci baki ɗaya bayu masu ɗauke da alhakin tsaron gidan sun fatsama neman Falmata lungu da saƙo na gidan ƙarƙashin umarnin Biyamuradi . Kasa zama Youssouf yayi ya kama hanyar komawa sashin sa zuciyar sa cike da fatan zuwa ya tarar da ita a inda jiya ta shiga ta ɓuya . A bakin ƙofar sashin suka ci karo da Siyama wacce ta ci kwalliya cikin riga da zani na wani sassalkan leshi sai zuba ƙamshi take fatar ta na ƙyalli . Da fara'a ta tare shi zuciyar ta da koyaushe ke kwaɗayin ganin sa tana cika da farin-ciki . Sai dai ga mamakin ta bai ko saurare ta ba ya wuce ta da sassarfa da alamun rashin nutsuwa a tare da shi . Da sauri ta taka ta bi bayan shi bayan ta ɗauki Yumna da tasan ba zata iya sauri ba . "Baban Yumna lafiya kouwa ? Me yake faruwa na gan ka haka hankali tashe ? "Wai Fatima-zahra ta ɓace tun jiya ba'a gan ta ba . Ya furta hakan lokacin da yake ƙarasawa gaban bishiyoyin da a jiya ta ɓuya bayan su , bai jinkirta ba ya tsallaka bayan bishiyoyin yana ƙiran sunan ta da wani irin sauti . Sasakai! Siyama tayi tana cikin yanayi mai kama da almara wai Fatima ta ɓata shi kuma Youssouf ya zo neman ta nan bayan shukoki anya Youssoufa ba matsala ya samu cikin ƙwaƙwalwar sa ba ? idan ba haka ba me zai kawo Fatiman nan bayan shuke-shuke'? Haka ya gaji da bankaɗa ganye ya fito jikin sa duk ya ɗau ƙura idanun sa sun yi jawur . "Baban Yumna Fatima kake nema anan kuma ? Cikin duƙusasshiyar murya yayi mata nuni da wajen yana cewa "anan jiya mun ka shiga ɗaki mun ka bar ta, kafin zouwan ki ina tare da itta a can Ya ƙarasa zancen da nuna mata bakin barandar sa kafin ya ɗora da cigaba da cewa " Ina Fatima zata sake tafiya ta bar ni ? Kamar ruwa ya cinye ta Siyama tayi shiru , zuwa yanzu ta fahimci abunda yake nufi da neman ta anan ashe ma jiya sun haɗu har sun gana? Ita har sokuwar zuciyar ta ke kambama ta a matsayin wacce ta fara kasancewa da Youssouf ɗin a jiya ashe hasashen ta bai zama gaskiya ba koyaushe alfarmar Fatima take ci daga wurin sa muddin ta samu cikakkiyar kulawar sa to Fatima ce ta mata tubalin ginuwar farin-ciki da nishaɗin sa . Bata ankara ba ta ga ya sake wuce ta yayi hanyar fita daga sashin nasu , da sassarfa ta bi bayan sa . Bayan kamar awa biyu labarin ɓatan Falmata ya fara zagaye masarautar bayan shafe fiye da awa guda da bayun gidan suka yi suna neman ta a cikin gidan amma ko wanda yace ya gan ta ma ba'a samu ba bayan masu gadin shiyar Youssoufa da suka bada tabbacin shigar ta da fitar ta daga sashin . Zaman dirshan Youssoufa yayi a falon Hajiya Umma yana jin wani irin bugu da ya wuce ƙima da zuciyar sa ke yi . Hajja kuwa zuwa lokacin ta fara sharar hawaye da gefen mayafin ta . Ubbo wacce take cike da takaicin damuwar da ɗan uwan ta yake shiga ta sanadin Falmata tace "To wai za ta ɓata ne ? Sai dai idan da ƙafafun ta ta fice doumin kouwa ai hakan bai zama sabon abu ba wajen ta . Kallon ta Youssouf yayi zai ce wani abu Hafsatouwa wacce ita ce ƙarshen dawowa daga neman Falmata da aka fantsama su tayi gurfano a gaban su hannun ta riƙe da cukurkuɗaɗɗen Mayafi. Da hannu biyu ta miƙawa Youssoufa kafin ta ɗora da cewa " wannan mayafin can wajen ƙofar fita gida ta ɓangaren kudu na tsinto shi wanda kuma nayi hasashen ya..... Miƙewar da Youssouf yayi riƙe da mayafin ya sa ta yin shiru duk suka zuba masa ido . Yana riƙe da mayafin ya kai shi ga hancin sa yana shinshinawa kafin ya ɗago kan sa da wani irin sauti yace "lalle wannan shine Mayafin da ta rufu da shi a jiya . Ita ma Hajja gyaɗa kai tayi cike da tabbatarwa tace "ƙwarai wannan mayafin Fatima ne to ita tana ina ? Muryar Hajiya Mama da ta ratso wajen ta katse musu hanzari inda take cewa "wannan alama ce da take nuna yarinyar nan an fita da ita daga gidan nan ne ta ƙarfin tsiya kuma babu makawa sace ta aka yi . Wani ƙaƙƙarfan kuka Hajja ta sa wanda ya ratsa zuciyar Youssouf ya tarwatsa duk wata nutsuwa da ta masa saura . "Innalillahi wa inna ilaihi raji'oon yanzu wanne azzalumin ne ya ɗauke yarinyar nan a wannan yanayin da take ciki na shiga uku ni hauwa'u 'yar mutane ta ɓata a hannun mu . Hajja ta furta hakan tana rufe fuskar ta da mayafin ta ta shiga rera kuka . Shigowar Babbar jakadiya yasa kallon su ya koma kan ta , saƙon Maimartaba ta isar inda take shaida musu kan cewa baki ɗaya yana neman su a shiyar sa a yanzu-yanzu da gaugawa. Ba a ɗau lokaci ba dukkanin su daga kan Hajiya Umma , Hajiya Mama da su Ubbo duk suka cika falon Maimartaba suka yi zaune suna sauraron sa . Bayan duk sun nutsu yace "wani labari ya zo mana Fada kan cewa wannan ɗiya ta Nigeria ta ɓata a cikin gidan nan yaya gaskiyar lamarin yake ? Shiru duk suka yi kafin Hajiya Umma tace "Hakane ran ka ya dade amma duk cikin mu babu wanda yake da masaniya kan haƙiƙanin yaya lamarin ya kasance domin ba'a gan ta a gida ba ba'a ga kuma wanda ya ce ya ga ficewar ta ba . "Rashin tsaro a gidan har ya zama haka da za'a nemi mutum sukutum a rasa ? Maimartaba ya furta haka da bayyanuwar matsanancin ɓacin-rai a fuskar sa . A hankali Ubbo tace "Ranka ya dade Allah ya daɗa maka nisan kwana ka cigaba da jagorar mu ni nafi tunanin Yarinyar nan ba ɓata tayi ba sai dai tafiya tayi da kan ta kamar yadda ta taɓa yi daga Niamey zuwa ƙasar su dan... Da wani irin sauti saɓanin wanda aka saba amfani da shi a masarauta yayin da ake gaban sarki Hajja tace " 'Yar nan wannan zancen naki ba gaskiya bane muddin kuma ya zama gaskiya to kune sanadi , saboda abubuwan da kuke yiwa yarinyar nan na tozarci kaɗai ya isa yasa ta zuciya ta bar gidan nan haba mana shin shi talaka ba mutum bane ? Ko kuwa laifin tayi domin ta auri ɗan uwan ku ? Fatima baiwar Allah yarinya ce ƙarama da take da larura wanda idan har baku gwada mata ƙauna ba bai kuwa dace ace kuna tozarta ta ba yanzu me za'a ce ga iyayen ta da kuka yi sanadiyar da ta gudu ba'a san halin da take ciki ba ?..... kasa cigaba tayi da magana saboda kukan da ya ci ƙarfin ta Hajiya Umma ta yunƙuro zata yi magana da hannu Maimartaba ya dakatar da ita . "Me yake Faruwa a gidan da ni ban kai ga sani ba ? Waye yake tozarta Al'umma ciki har ma da mutanen da suke amintattun mu da muka amso amarnar su daga hannun mutanen su ? Shiru aka yi babu mai tsaurin idon iya amsawa . Kamar daga sama Muryar Youssouf ta ratso wajen inda yake cewa " Fatima ba gudu tayi ba babu makawa ɗauke ta aka yi .. Ya ɗan jinkirta lokacin da idanun kowa ya dawo kan shi zuciyar Hajiya Mama ta fara sauya ƙarfin bugu tana dik-dik-dirim-dim. "Wa kake tunanin ya ɗauke ta ? Maimartaba ya furta haka cike da nazarin sa , Shiru yayi da yasa gumi ya shiga zarya ta cikin rigar Hajiya Mama . "Maimounatou . Ya furta hakan da tasowar matsanancin ɓacin rai a muryar sa , ya cigaba da cewa "Maimounatou ita ta sanya a zo a ɗauke Fatima domin cikar burin ta ta wani fanni sai dai a wannan karon ba zan kyale ta ba dole ne na gwada mata ainashin ɗabi'ar da na ɗau shekaru a wajen koyar ta cikin aikina na na soji . Muryar Hajiya Mama ita ta ratso wajen cike da wani boyayyen farin-ciki a sautin ta tace " Yarima ni da kaina tunanin da ya fara zowar min kenan ba shakka wannan ɗiyar ta Agades ita ta sanya anka ɗauke wannan yarinya ta ƙwarai kuma dole ayi hanzarin ɗaukar mataki akan haka. Shiru Maimartaba yayi cikin son yin nazari sai dai hayaniyar da ta fara tashi a tsakanin iyalan sa da duk suka aminta da cewa Maimounatou ce ta tura aka sace Falmata duk kuwa da babu hujja ɗaya da aka samu wanda yake bada tabbaci ga hakan ya dukusar da hanzarin sa musamman lokacin da Youssouf ya miƙe a safure ya taho gaban shi yayi gurfano . "Ranka shi daɗe zan tai Niamey yanzu zan tai na tadda Maimounatou ta faɗa min ina ta kai iyalina ? "Youssoufa ka nutsu wannan batu ne da yake buƙatar nutsuwa da tsawaita bincike , ina maka oumarni da ka jinkirta hanzarin da kake yi har a ƙarƙare bincike a samu madogara . Da kyar Maimartaba ya shawo kan hayaniyar su bayan ya tabbatar da za'a tsananta bincike kafin tunkarar koma waye da aka samu shaidar yana da hannu a ɓatan Falmata Bayan fitar su daga Sashin Maimartaba Hajiya Mama bata koma sashin Hajiya Umma ba kai tsaye sashin ta ta koma ba tare da ta zauna cikin 'ya'yan ta da suke ta hira kan batun ɓacewar Matar Youssouf da wasu daga ciki ma daɗin lamarin suke ji saboda ta riga ta gina ƙaƙƙarfar ƙiyayya tsakanin su da Youssouf da duk wani abu na bakin-ciki da zai faru da shi su murna suke yi . Can ƙuryar ɗakin ta ta shiga ta fara kai kawo cike da tunanin kan mataki na gaba da zata ɗauka wajen cigaba da tsare Falmata dan kada a samu wani lamari ya gifta da asirin ta zai shiga hatsarin tonuwa A ɗan firgice ta waiga jin motsin shigowa ɗakin Hafsatouwa ce ta ƙaraso gaban ta da sassarfa bayan ta rufe ƙofar . "Hafsatouwa sirrina yana cikin haɗari ya zama dole ki shirya ki tafi Zuru wajen mai jar-tawada ki amso min wani gagarumin aikin da zai kurumtar , ya makantar idan ya kama ya gurguntar da duk wasu da zasu iya kawo min tsaiko kan ƙudiri na ne ma duk ayi . " a min aikin da zai shafe tunanin ita kan ta yarinyar nan da ta san sirrin na sannan a mantar da duk wasu makusanta nata daga tunanin ta har sai lokacin da na gaji dan kaina da hukunta ta na sake ta , ke Hansatouwa ina so na zama ni nice , kowa kuma ya zama ba kowa ba , ina nufin kowa da kowa na cikin masarautar Maradi su dawo ƙasan iko na a baɗini da fatan kin gane ? Cike da jin tsoron yanayin da take hango uwargiyar ta a ciki hafsatouwa ta shiga gyaɗa kan ta . "Oumarnin ki abun bi ne ranki shidaɗe uwargijiya ta mai girma . "Da kyau to ya ya kin yi abunda nace kiyi ? "Ranki ya daɗe tuni nayi . "Kin ji motsin ta ko kaɗan daga inda take ? " ba wata alama dake nuni da cewa akwai rayayyen mahaluki a bigiren da alama yarinyar bata da taurin kai . "Idan ta yi haka ta sauƙaƙawa kan ta riskar wasu daga cikin tarin horon da nake mata tanadin su . "Kina iya tafiya yanzu , idan buƙatar son ganin ki ya zo zan aika a min ƙiran ki . " To ranki ya daɗe godiya nake . Gaf da Azahar bayan hankulan mafi yawan mutanen gida ya tafi ga haramar sallah Hajiya Mama ta kashe jiki ta nufi tsohon sashin babar ta kuma Uwargidan Sarki Azizou Baskore "Hajiya Uwa . Da tun bayan rasuwar ta sama da shekaru goma sha takwas babu wanda ya sake zama a sashin ya zama tamkar kufai , sai fa Hajiya Mama da jifa-jifa take zuwa sashin tana yin wasu abubuwan da ta ce raya sashin take yi da yake a matsayin na uwa a gare ta wanda kuma a baɗini daga Allah sai ita sai kuma tsirarun mutanen da tayi haɗakar ƙulla sirrukan ta da su , suka san ainashin abunda take aikata a sashin a duk ƙarshen kowanne wata . Bayan ta gama nazarin wajen ta tabbatar babu wani mahaluki a wajen da zai iya jin abunda za ta yi ta sanya ɗan makulli ta buɗe ƙofar falon bayan ta ɗau wata leda da take yashe daga kusa da ƙofar . Kan ta tsaye ta shiga falon ta tura ƙofar ta rufe tana mayar da ganin ta kan Falmata wacce take takure daga can gefe cikin datti da ƙurar da ta maye gurbin shimfiɗar ɗakin ya zama duk inda ka ɗora ganin ka datti ne da tankaɗaɗɗiyar ƙasa kamar an kwaso an zuba ba'a ko iya ganin ainashin dandaryar ɗakin . A hankali Falmata ta ɗago kan ta dake tsakanin cinyoyin ta da ta haɗa su ta takure ba'a ce mai ciki bace . Taku tayi ta ƙarasa gaban Falmata tashin sautin ta ya biyo bayan ledar da ta wurgawa Falmata " wataƙila kina jin yunwa ki ɗau abinci ki ci ya rage naki ki cinye shi duk ko kuma ki rage dan anjima . Falmata da fuskar ta ta kumbura saboda kuka ta buɗe bakin ta da take ji ya mata nawi muryar ta bata fita sosai tace "Sallah nake so nayi ki nuna min wajen da zan yi Alwala . Wani kallon banza Hajiya Mama ta mata kafin ta ƙuta , sai da ta mula sannan tace " ga rairayi nan kina zaune a cikin sa ki buga ƙasa kiyi taimama . Bata jira ba ta cigaba da cewa " ina sake jaddada miki muddin kina son tsira da rayuwar ki to ki kiyaye abunda zai sa a san kina nan , idan kuwa kin ƙi ji .? Da zubowar sabbin hawaye Falmata tace "Hajiya Dan Allah ki tausaya min , ki ji tsoron Allah mahalicci da yake kallo tare da jin kowa da kome , ban yi miki kome ba ..... "Ke . Hajiya Mama ta daka mata tsawar da ya sa Falmata yin shiru " kina son karya doka ta ne ? Da sauri Falmata ta girgiza kai . "Tashi , tashi nace ko ? Da kyar Falmata ta miƙe saboda ƙafar ta da ta ji ciwo a jiya ga yunwa da ƙishirwa , sun sa har jiri take ji bayan ciwo mai tsanani da kan ta yake yi , ta ɗingisa dakyar ta bi bayan Hajiya Mama wacce tayi gaba zuwa wata ƙofa ran ta cike da fatan "Allah yasa afuwa zata mata ta fitar da ita daga wannan wajen . Da kallo ta bi ɗakin da su shiga wanda ba kome a cikin sa bayan tulin ƙura da yanar-gizon da ya zarta na falon sai fa wani karmamin gadon katako da duk gara ta cinye shi shi ɗaya ƙwal a ɗakin. "Anan za ki cigaba da zama , ga banɗaki nan a ciki amma bani da tabbacin rasa macizai da kunamu a ciki sai ki kula wajen amfani da shi idan ba haka ba kin ga sun hutar da ni daga kashe ki. Daga haka Hajiya mama ta juya da kusan tare suka juya da Falmata wacce ta zube a ƙasa tana wani irin kuka ta riƙe ƙafar Hajiya Mama tana shisshiƙa kamar ran ta zai fita tace "Hajiya Dan Allah , Allah ..... Hanɓare ta Hajiya Mama tayi ta taka da sauri kafin Falmata ta yunkura ta fita ta rufo ƙofar ta murɗa ɗan makulli . Tare suke da page 51b [2/27, 9:35 PM] +234 706 503 6187: MAFARI ( hargitsin Rayuwa ) Umm"muaz 51b Duk yadda Maimartaba yake tunanin za'a yi samu wata alama da zai nuna ina Falmata take anyi amma babu nasara har aka kwana aka yini babu wani bayani takamaimai na inda take . Zuwa lokacin kuwa Biyamuradi Youssouf gaba ɗaya ya gama birkice musu ya kuma matsa lamba kan son zuwa Niamey wajem Maimounatou dan ta faɗi inda ta kai Falmata. A ƙarshe ba yadda maimartaba ya iya ganin yadda ɗan nasa ya zama yasa ya masa umarnin tafiya bayan ya masa nasiha akan haƙuri da mallakar zuciyar a duk lokacin da rai ya ɓaci sannan ya gargaɗe shi da gujewa ɗaukar mataki cikin fushi . Ƙarfe goma na ranar jirgi ya ɗaga da shi da Bilal da zai masa rakiya zuwa Niamey . Bayan tafiyar Youssouf Hajiya Mama ta ƙira Hafsatouwa ta umarce da cewa gobe da sassafe ta kama hanyar Zurun Jahar kebbin Nigeria bayan ta danƙa mata isassun kuɗin da zasu ishe ta . Duk da cewa Falmata baƙuwa ce a masarauta Maraɗi amma hakan bai hana masarautar ta zama cikin alhini ba kasantuwar ta riga ta zama wani ɓangare na gidan , ko'ina ka ratsa za ka ji bayun gidan suna batun ɓacewar Gimbiya Fatima da cikin jikin ta . Hajiya Umma da kan ta ta shiga damuwa musamman da ya zama Maimartaba yana ganin har da sakacin ta wajen ɓatan Falmata da har a jiya da dare ya tabbatar mata da hakan cikin fushi . Hajja kuwa ƙurewar tashin hankali ta shiga tayi kuka har ta bawa aku lada ta haƙura ta rungumi charbi tana addu'ar Allah ya baiyana mata uwarɗakin ta a halin lafiya . Niamey . Lokacin da Youssouf ya isa Niamey daga airport kai tsaye babban ofishin 'yan sanda ya nufa inda har lokacin ake cigaba da tsare Mammadou da Maimounatou sakamakon rashin sanin halin da shi yake ciki da hakan ya kawo jinkirin miƙa su kotu a musu hukunci . Bayan ya cike takardu aka masa iznin ganin su da Mammadou ya nemi ganawa a farko . Lokacin da aka fito da Mammadou , Youssouf da yake zaune bai san lokacin da ya miƙe ba da sauri ya taka ya taro Mammadou da yake tangaɗi , ba tare da ya damu da tsami da warin da yake tashi daga jikin Mammadoun ba ya kama shi suka zauna . Da wani irin yanayi a fuskar sa mai tsauri yace "Mammadou ƙaƙa ka zama hakka ? Shin baka da lafiya ne ? Ko kouwa horo ake maka ? Mammadou da zuciyar sa ta cika taf da farin-cikin ganin Youssouf ya riƙo hannuwan sa duk biyu kafin ya fashe da matsanancin kuka cikin kukan yake cewa "Youssoufa kai min gafara , ka yafe min ɗan ouwana na tuba ka yafe min , nayi nadama marar amfani na kouma yi tir da muguwar uwa irin tawa tare da..... Da sauri Youssouf ya katse shi yana cewa "Mammadou kar ka tsawaita zance domin ba shi da wani amfani dan kouwa ba zai yi gyara cikin abun da ya wouce ba kouma zouwa ma nayi mu tai gida tare nan ba wajen yin zance bane Mammadou . Cikin wani irin sauti Mammadou yace "da gaske Youssoufa zowa kayi ka tafi da ni gida ? Miƙewa Youssouf yayi yana zube hannuwan sa cikin aljihu ya fara taku yana barin wajen ƙarƙashin rakiyar idanun Mammadou da ya bi shi da kallo sai da ya kai ƙofar ficewa daga wajen bai jiyo ba yace "ƙwarai yau kake kwana a gida Mammadou . Daga haka ya fita yana jin yadda tattaurar zuciyar sa ke son tasowa ta hana shi duk wani afuwa da sassauci da yayi niyyar yi ga ɗan uwan nasa . Ya juya baya ga ƙofar shigowa lokacin da aka taso ƙeyar Maimounatou ta shigo inda yake idanun ta da suka shige ciki ta ware tana kallon sa a take ta shaida ko wanene a gaban ta , sannan 'yar murna da ta fara safko mata jin cewa an zo ganin ta ta koma ciki fargaba mai girma ya mamaye ta da yasa har wasu siraran gumi suka fara tsiyaya ta cikin rigar ta . cikin raggon taku ta nufi inda yake sai dai kafin ta ƙarasa ya juyo baki ɗayan sa yayi tsaye ƙem a gaban ta da juyowar sa tayi hanzarin sauƙe idanun ta ƙasa tana jin wani yanayi da ta gagara tantance a wanne matsayi zata ajiye shi "kunya ce ? "Nadama ce ? Ko kuwa tsoro ne ? Bata ankara ba ta gan shi daf da ita kamar an tunkuɗo shi hannuwan sa zube cikin aljihun wondon sa da sautin sa mai amo da ya sake kaurarara yace "Madame, êtes-vous surprises ? Wani murmushin yaƙe Maimounatou tayi da ya taho da ɗoyin da bakin ta ke yi , ta ɗago kan ta ta saci kallon sa kafin ta wani karya kai gefe ɗaya cikin muryar da ta saba hilatar sa da shi wacce yau ta sake matsewa tace "Pas vraiment, tu ne m'as pas surpris, je sais que tu reviendras vers moi. Hannun ta ta miƙa da nufin taɓa shi ya jaa baya da sauri yana kokuwa da ɓacin ran sa da idanun sa da suka yi jaa ya mata wani kallon gargaɗi da ya kaɗa mata ciki . Da baya-baya ya dangana da kan kujerar da take gaban ɗan teburin da yake cikin ɗakin ya zauna yana harɗe ƙafafun sa ɗayan kan ɗaya yace. " idan kin ka yi tounanin kina da watta sauran dama guda da ta rage miki a gareni kin yaudari kan ki yau ba rana ce ta wassa ba don haka Arrêtez de jouer avec votre propre cœur et de vous dupe. Wani murmushin ta sake yi kafin ta yi ɗan taku kaɗan tana juya baya ga barin fuskantar sa cikin ƙarfin hali tace " Bana neman watta dama dagga gare ka a yanzou sabbada kuwa duk watta dama na riga na same ta har ma...... Tsawar da ya yi haɗi da buga teburin gaban sa shi yasa ta juyowa a firgice , a tsaye ta gan shi fuskar sa da ta duba a lokacin ji tayi marar ta ta cika fam. Ya matso daf da ita yana nuna ta da yatsan sa ya ce "kadda ki min wassa , ni damisa ne da ban juri wasa ba ban ɗauki wargin mazaje ba a fagen daga na sanya bakin bindiga na fasa ƙoƙon kan su na sa ƙafafu na taka cikin su kar kiyi zaton zan miki sassauci , hannun sa ɗaya da yake cikin aljihun sa ya zaro da yake riƙe da ƙaramar bindiga , yayi taku kaɗan zuwa baya kafin ya cigaba da cewa "zan iya tarwatsa kan ki da harsashi bayan na tattaka ki muddin kin ka cigaba da min fi'ili . Kafin ya mayar da numfashi Maimounatou ta zube akan guiwowin ta ta haɗa tafukan ta biyo tana sakin wani mitsi-tsin kuka mai tafe da sautin tsoran da ruhin ta ke ciki tace jikin ta na ƙyarma tace , " Dan Allah kayi haƙuri kar ka kashe ni , wallahi sharrin shaiɗan ne ya sa na aikata abun da na maka ka yafe min . Wani guntun murmushi Yayi kafin tace "Ashe kina tsoron Mutuwa ? Ni kuma kin ka nemi kashe ni ? Babu yafiya a tsakanina da ke ko afuwa ba zan iya miki ba muddin baki sanar dani dalilin da yasa kin ka nemi raina ba? Da sauri Maimounatou tace "wallahi zan faɗi dalili . Komawa yayi ya zauna yana ƙoƙarin sassauta fushin zuciyar sa yace "Vous avez seulement 30 minutes. Kamar an kunna radio Maimounatou ta shiga ba shi labari tiryan-tiryan tana yi tana kallon sa tana karya wuya da sharar hawaye . Bai katse ta ba har sai da ta kai ƙarshe Kan sa a ƙasa yace "menene gaskiyar cewa da kika yi Mammadou ya kawo gubar da kin ka ciyar da ni ? Girgiza kai tayi cikin ƙaramar murya tace . "ba shi bane ni na aiki Gnala ta sayo min . sannan cikin kuka ta cigaba da cewa "Amma wallahi nayi nadama iyakar nadama dan Allah ka min afouwa ka sake bani dama na gyara kuskurena wallahi wannan karon da dukkanin zuciya ta zan zauna da kai zan tallafi soyayyar da kake '..... Ɗago da kan sa da yake sunkuiye yayi yana ɗan buga tafin hannun sa akan teburin gaban sa yayi wani murmushi mai ciwo . "Soyayya ? Yanzu kina zaton har kawo yanzu akwai sauran ɗigon na alamar son ki a raina ? Bayan duk abun ƙi da kin ka wanzu wurin aikata shi a gareni.. Huci yayi yana danne ƙiyayyar ta da yake ji mai karfi tana naso a cikin ran sa daga lokacin da ta ambaci sunan Ghaddafi Yacouba Dango a matsayin mutumin da ta nemi kashe shi a kan sa bayan irin ha'intar sa da tayi ta dunga yaudarar sa da sunan soyayya har ya aure ta bayan sun gama tanbaɗewar su da wannan riƙaƙƙen ɗan ta'addan haƙiƙa Maimounatou guba ce ba domin yana yaƙar zuciyar sa da babu abunda zai hana ya harbe ta a lokacin . Ya tsaya faɗa mata matsayin da take kai a wajen sa a yanzu tamkar ɓata lokaci ne ko kuwa bata wani matsayi na daban da ya wuce wanda takai kai yanzu a wajen sa dan haka ya mayar da ganin sa gefe daga kan fuskar ta da alokacin yake ganin ta da muni fiye da duk wani mummunan abu da ya taɓa cin karo da shi a tsawon rayuwar sa . "Ina kin ka sa a ka kai Matata ? A dabar-barce Maimounatou tace wacce matar ka ? Taku ɗaya yayi ya miƙa hannu ya figo ta tayi zaman 'yan dabaro a gaban sa ya shaƙe wuyan ta kafin ya danna mata bakin bandiga akan ta wata irin razananniyar tsawa ya daka mata yana sake maimaita tambayar ta. " Ina ki ka kai Fatima-zahra Mata ta nace ? Ki faɗa min ko na fasa kan ki . Baki ɗayan jikin ta ɓari yake ta kasa magana saboda maƙogoron ta da ya shaƙe ya sa ta fara jin ƙamshin mutuwa . Ta kai mintuna biyu a haka a shaƙe a hannun sa , sai da yayi da gaske tukun ya iya haƙura ya sassauta shaƙar da ya mata ya ingiza ta ta faɗi . Kan sa ya sake sauƙewa ƙasa yana huci bai ɗago ba yace " za ki faɗa min ko kuwa na kashe ki ? Tana wani irin kuka Maimounatou tace "wallahi Allah ɗaya kenan bani da watta masaniya kan ɓatan ta . Cikin tsawa yace "to waye zai sace ta? Waye maƙiyi na da ya wucce ke ? Ina da wani Maƙiyi bayan ki ? Za.... "Wallahi kana da Maƙiyiyar da ta wucce ni wacce ita tayi sanadin faruwa duk wassu abubuwa marasa kyau da sun ka samu rayuwar ka . "Wacece itta ? Ya tambaye ta a daƙile Da sauri ta amsa masa da "Hajiya Mama. Yamutsa fuska yayi kamar yana son tuna inda ya taɓa jin sunan . Ganin haka ya sa Maimounatou cigaba da cewa " Baka da wata maƙiyiyar da ta wuve Hajiya Saratu , Matar Mahaifin ku Mahaifiyar Mammadou Hajiya Mama. "Ita ta wanzu tsawon shekaru tana bin ka da sharri da ita da Tsohuwar Matar kakan ku Hajiya Uwa su biyun sune suka fara lalata rayuwar ka ta hanyar yi maka mummunan sihiri, " su suka sa ka zama mashayin giya "giyar burkutu , su suka sa kayi zina da yarinya Amina wacce take 'yar uwa ga ɗaya daga cikin matan da za ka aura, Su suka yi ma Asiri tun kana ɗan shekaru biyar bai fara aiki ba sai da ka shekara goma sha takwas , ranar da ka cika shekaru goma sha takwas a ranar ka fara shan barasa, ranar da ka cika shekara talatin a ranar ka fara yin zina a kuma ranar ...'' Ɗago ta Youssouf yayi ya haɗa ta da jikin bango gaba ɗaya jikin sa tsuma yake cikin ɗimauta yake cewa "ƙarya kike yi , ke maƙaryaciya ce maha'inciya munafuka ki faɗa min gaskiyar aina duk kika samu wannan bayanin ? . Idanun Maimounatou sun fito waje amma bata haƙura da magana ba ta cigaba da cewa " kuma Hajiya Mama bata daina sabunta aikin asirin ba ko bayan mutuwar Hajiya uwa babban burin su ka rasa ƙima da darajarka ta ɗan sarki da hakan zai sa ka gaza wajen hawa kujerar mulkin Maradi , a wayi gari Mammadou shi ne Sarki. "Duk abunda nake faɗa maka a yau gaskiya ne babu ɗigon ƙarya ko ɗaya a ciki, ita da bakin ta ta faɗa min idan kuma kana son samun tabbaci da kuma hakan zai kai ga karya duk wasu sihiri da aka maka kuma har yau suke aiki a kan ka , ka koma Maraɗi ki tafi tsohon sashin Hajiya Uwa a babban falon ta cikin ɗaki na biyu daga hannu hagu ka bincika ɗakin a cikin armoire asirin da aka maka yake . " Ka je ka fasa kome , Ka ɓata kome , muddin kana son cigaba da yin rayuwar da babu dabaibayin sihiri a cikin ta . "A ƙarshe ina baka tabbacin Hajiya Mama tana da hannu wajen ɗarsuwar duk wani baƙin-ciki a rayuwar ka dan haka ba tamtama a wannan karon ma ita ta sace Fatima . Sakwaf ! Youssouf ya sake ta ta faɗi a ƙasa kalamanta na ratsa duk wasu jijiyoyin cikin ƙwaƙwalwar sa suna aikawa da saƙon gaugawa zuwa cerebrum na kwakwalwar sa har zuwa temporal lobe da anan take ya fara ƙoƙarin tuno masa da duk wasu motsi da lamurarran Hajiya Mama a kan sa . "Yadda take kyarar sa tun yana ƙanƙanin sa , da ya fara girma ya mallaki hankali sai yana lura da ko ganin sa bata son yi sannan duk wani abu na farin-ciki idan ya same shi bata taya shi murna haka kuma na baƙin ciki , kai ko jinyar da yayi na kwanan nan ma bata taɓa masa ya jiki ba , bare ta jajanta masa , a duk lamuransa idan ba ɓacewar Falmata ba bai taɓa jin ta sanya bakin ta ciki ba ya daɗe da sanin bata ƙaunar sa . "To amma anya hakan ya isa ya sa shi yarda da cewa Hajiya Mama Matar Mahaifinsa ita ce ta sace Matar sa ? Girgiza kan sa yayi yana jin haɗuwar kalaman su su biyun masu cin karo da juna a can Maradi Hajiya Mama tace Maimounatou ce ta sa aka ɗauke Fatima , anan kuma Maimounatou tace Hajiya Mama ce ta sa aka ɗauke Fatima . "Waye mai gaskiya a tsakanin su ? Abu mafi girma da ya fahimta a tsukin lokacin shine wata ɓoyayyar alaƙa da take tsakanin su biyun da bai taɓa kaiwa ga sani ba . Kalaman Maimounatou akwai ɓurɓushin gaskiya a cikin su Musamman cikakken bayanin da tayi masa kan lokutan da munanan al'umuran da suka faru a rayuwar sa suka fara faruwa . "Ya zama dole na koma Maradi , na koma domin samun tabbaci tsakanin ƙarya da gaskiya . Da sasaarfa ya juya yana barin wajen , Maimounatou da take zaune dirshan a ƙasa tana mayar da numfashi cikin wata irin murya tace "Youssouf ka min afouwa ka yafe min ka sake bani dama . Tsayuwa yayi ba tare da ya juyo ba yace "Na sake ki saki Ukku Maimounatou kada kuma kiyi fatan abunda zai sake nuna mana fuskokin juna a zahiri . Ihun da Maimounatou ta sa sai da ya ƙarade harabar ofishin kafin ya bar da'irar wajen yana iya jiyo hargowar ta tana ƙiran sunan sa . "Youssoufa. "Youssoufa ka dawo wallahi nayi nadama . Bata taɓa sanin cikin wasanni ta ta haɗo da zuciyar ta ba sai a yau da Youssoufa ya rayu bayan so da tayi ta gille masa rayuwar sa ya kuma dawo ya sake ta irin sakin da babu kome , a dai-dai lokacin da ita kuma zuciyar ta ta haƙaƙe da cewa ta daɗe cikin mayen son sa tun tana ƙaryata kan ta akan haka har a ƙarshe ta saduda ta kuma shiga addu'a ka'in da na'in Allah ya tashi kafaɗun sa ya dawo su cigaba da rayuwar su . haƙiƙa tayi asarar Miji irin wanda ba zata samu madadin sa ba . To wa ma zai sake auren ta ? Kenan ita bata ci ribar kome ba sai fa ta lalacewar suna a idanun al'umma ta zama mujiya abar zunɗe . Zuciyar ta taji tana wani irin narkewa da nadama marar iyaka , tsoron halin da zata tafi ta tadda a rayuwar gidan su na huda ta da tun da ta kwashi tsawon satika bakwai a kulle babu wanda ya leƙo daga gidan su ko wani dangi nata ta san cewa kurar ta tayi kuka ta kuma riga ta dusashe tayi duhu a idanun kowa na ta . Kwanciya tayi a ƙasa tana wani irin kuka tare da jin yadda zuciyar ta ke zogi kamar zata fashe a tsukin lokacin zaɓar mutuwa take son yi akan rayuwar da zata tarar a gaba . Kai tsaye Youssoufa ainashin cikin ofishin ya koma inda ya nemi da a ba shi takaddun neman belin waɗan da ake tsare da su . Baya cikin nutsuwar sa ya ciccike inda ya bada tabbacin yin afuwa ga Masu laifin su biyu da ake tuhuma da yunƙurin kashe shi a matsayin sa na wanda suka yiwa laifin ya sanya hannun ya janye ya musu afuwa a sake su . Bayan gajerar muhawarar da Youssouf bai bada hankalin sa ba ya ƙirgo wasu kuɗaɗe ya ajiye a gaban teburin ya miƙe yana barin wajen bayan sun yi Sallama. A waje ya tarar da Bilal cikin motar direban da Mijin Ubbo ya turo ya ɗauke su idan sun gama bai shiga motar ba ya ƙira Bilal ya fito . "Ka shigga ciki za'a fito da Mammadou ku tafi gidan ubbo tare ni akwai inda zan tai . Bai jira amsar sa ba ya taka da sauri yana barin wajen . Wani ƙaramin Hotel ya je ya kama ɗaki na kwana guda (HOTÈL TÉNÉRÉ) tun da ya shiga ɗakin ya kashe wayoyin sa yayi sallah yayi zaune tunaninnika na masa rubdugu . ji yake kamar ya buɗi ido ya gan shi a maraɗi wani irin hali ya kasance a ciki tsawon ƙarshen yinin zuwa cikin daren da ya tsinci tsawon sa fiye da na darare uku a wajen sa . Asubar farko ya miƙa mukullin ɗakin ya bar otel zuwa tashar mota . Mota ta farko da ta tashi zuwa Maraɗi da misalin ƙarfe shidda na safe cif sun kama hanya tare da Youssoufa da ya kasa jiran karfe biyun ranar jirgi ya tafi da shi . Ya zaɓi tafiyar motar saboda ya san duk inda ƙarfe biyu na ranar tayi yana cikin Maraɗi . Maradi . Tun ajiya da Hajiya Umma da shi kan sa Maimartaba suka kasa samun layin Youssoufa suke cikin fargaba duk kuwa da cewa sun yi waya da Bilal har ma da Mammadou cewar suna lafiya kuma Youssoufa ma yana lafiya sai dai su ma basu san inda yake ba kuma basu samun wayar sa. Bayan addu'a babu abunda Hajiya Umma take yi saboda jikin ta yana bata wani abu ya faru ko kuma zai faru ko mai kyau ko marar kyau . kuma kawo yanzu ta fahimci ƙaunar da ɗan ta yake yiwa Falmata marar misaltuwa ce ba yadda ta iya dan dole ta fara addu'ar Allah ya bayyana Fatima ko dan Youssouf ya samu nutsuwa . Ga Hajiya Mama kuwa yau ranar farin-ciki ce a wajen ta dan kuwa har 'yar ƙaramar walima ta haɗa na farin-cikin dawowar ɗan ta mafi soyuwa a wajen ta da aka yiwa sharri aka garƙame ta gayyaci ƙawayen ta na ƙud da ƙud dan su zo taya ta murna . Matar Mammadou da ake ƙira Zainaba ita ma a nata gidan sai murna tare da shirin taryar Mijin ta . Kamar kullum yau ma bayan an tafi Sallar Azahar Hajiya Mama ta kashe jiki ta nufi shiyar Hajiya Uwa ta buɗe ta shiga . Ƙarfe biyu saura mintuna goma taxi da ta ɗauko Youssoufa daga tasha ta sauke sa baya cikin nutsuwar sa ya biya mai taxi . Da sassarfa yake taku ya nufi cikin gidan kallo ɗaya zaka masa ka matsa daga hanya ko da kuwa ba ka san ko shi wanene bane . Ta gaban Fada ya zo ya wuce akan idanun Maimartaba da kowa na cikin fadar wanda hakan shine na farko da Youssoufa ya zo ya wuce ta gaban Mahaifin sa bai ƙarasa ya gaishe shi ba , abu ne da bai faruwa mutum ya taka ƙofar fada bai shiga ya kai gaisuwa ba . Shiru Fadar ta ɗauka kafin cikin abunda yake ƙasa da mintuna biyu wani daga cikin manyan bayun gidan ya taho a sukwane ya yi gurfano yana kai gaisuwa kafin ya ɗora da cewa "Ran Sarki ya dade yau da alamun ɓacin-rai mai girma ga Yarima Biyamuradi domin kuwa ga shi can riƙe da bindiga a tsirarar ta ya nufi shiya...... Miƙewar da Maimartaba yayi babu shiri ita ta sa sauran 'yan Fada suka miƙe tsaye su ma su na cewa "Allah ya huci zuciyar ka jagoran Al'umma Yaa Sarkin mu mai Adalci . Cikin ɗago taku Sarki Abdoul-azizou ya wuce gaba bayan yace "mu tai ka min jagora zuwa inda yake . Hajiya Mama da Biyamuradi Youssouf ƙiris ya rage su ci karo a tsakanin hanyar sashin Hajiya Uwa , ita tana fitowa shi kuma yana ƙoƙarin shiga da sauri ta jaa baya idanun ta a waje take bin sa da kallo . Shi ma tsare ta yayi da ido yana bin ta da wani irin kallo mai kaifi da yasa nan take laɓɓan ta suka ɗauki rawa kamar wacce take gaban alƙali . "Kai..kai kuma la..lafiya ? Ina..ina za ka tai ? Bai amsa mata ba ya wani irin kewaye ta ya wuce , wani mummunan bugu zuciyar ta ta hau yi ganin inda ya nufa kai tsaye ƙofar falon Hajiya Uwa . Taƙi barin fargabar da take bin duk lakkar jikin ta tana kassarawa tayi nasarar duƙusar da hanzarin ta , ta bi shi da ɗaga takun da ta ƙara da gudu ta sha gaban sa lokacin da yake ƙarasawa gaban ƙofar ta shiga tsakani sa da ƙofar ta raba hannuwan ta cikin wata irin buɗaɗɗiyar murya tace " Ba zaka shiga ba ka koma inda ka fito nan ba hurumin ka bane , nace ka koma. Idanun sa da suka yi jawur ya ɗago yana kallon ta da wani irin yanayi da ya fara fita a saiti na hankalin sa ya sanya hannun sa ɗaya ya ture ta gefe tayi taga-taga zata faɗi amma ta tokare. Sai dai me ? Ture ta da yayi da ƙarar ɓalla ƙofar da yayiwa duka ɗaya da kafar sa ya shiga falon basu ruguza mata zuciya kamar taron mutanen da ta hango sun yi ɗango suna tahowa ba wanda halin ɗimuwar da take ciki bai hana ta gane Maimartaba , Hajiya Umma tare da kakaf 'ya'yan su da suke gida a dai-dai lokacin zuwa manyan bayu da ma ƙanana da suke danno musu baya ba . Jin ƙarar kamar Youssoufa yana karya wata ƙofar ya sa ta runtumawa da gudu ta faɗa falon ba tare da ta damu da taron mutanen da suke iya hango duk abunda yake faruwa ba , hankalin ta a dai-dai lokacin ya kasa yarda da abunda ke shirin faruwa da ita . Tana shiga ta riƙo rigar Youssoufa ta baya tamau ta cukuikuye shi ta hana shi shiga ɗakin da ya riga ya karya ƙofar kawai sai ta saki wani irin ihu dai-dai da shigowar Maimartaba . "Maimartaba ka hana shi ka hana shi nace wayyo Allah na , nace ka hana shi kar ya min lahani ga rayuwa ta. Wata irin fincika da Youssouf ya yiwa rigar sa sai da ya kai Hajiya Mama ƙasa da sauri Hajiya Umma ta tare ta cikin ɓacin rai tace "Kai Youssoufa mene ne kake yunƙurin yi hakka ? Hala bakka cikin hayyacin ka ? Bai saurari kowa ba sabod idanun sa daga na zuci har na zahiri a makance suke.a lokacin ƙudirin da yake gaban sa kawai yake son cimmawa . Yana danna kai a ɗakin ya shiga yin fatali da duk abunda ya tarar a cikin ɗakin da bai wuce wasu itatuwa da wasu ƙwarrai da babu kome a cikin su ba. Dube-dube ya shiga yi har idanun sa suka sauƙa kan wardrobe irin ta jikin gina na shekaru aru-aru . Duk da ƙarfin da yake da shi da jarumta irin na sojin ƙwarai da kyar ya iya buɗe ta ya shiga yawo da idanun sa a ciki lokacin da Hajiya Mama ta sake yin kukan kura ta kufce daga Hannun Hajiya Umma ta faɗa ɗakin . Idanun sa suna sauƙa akan wata ƙatuwar ƙwarya da take ajiye daɓas da duwawun ta bata wani tangaɗi ba'a ce ƙwarya bace lokacin kuma Hajiya Mama ta sake riƙo rigar sa ta baya cikin wata irin murya mai firgitarwa tace " Kar ka taɓa , wallashi ina kashe ka idan ka taɓa . Kalmomin ta suka sauƙa a kunnuwan Maimartaba da Hajiya Umma da suke shigowa ɗakin sauran mutane na biye da su domin kowa ya shiga ɗimuwa tare da ƙaguwa kan son fahimtar wai me yake shirin faruwa ? Hannun sa biyu ya sa ya cicciɓi ƙwaryar yana juyowa Hajiya Mama ta jawo rigar sa da iyakar ƙarfin ta da har sai da ta ɓarke . Ƙwaryar kuma tayi tangal-tangal a hannun sa lokaci ɗaya ya sake ta ta tafi baki ɗaya ta kwaranye a rabin jikin Hajiya Mama kafin ta kai ƙasa ta tarwatse . Wani fitinanne wari marar daɗi da yake tada hankali ya cika ɗakin da yasa sai da kowa ya toshe hancin sa wasu suka yi baya da sauri . Maimartaba da yake tsaye ƙiƙam da idanu ya bi wasu kwaɗi biyu da suka fito daga cikin ruwan mugunyar sai tsalle suke suna neman wajen ɓuya . Kafin yayi wani yunƙuri Liman da shi ma hankalin sa ya kai kan su nan take ya fara addu'a . Chak suka tsaya suka bar tsallen yayin da warin da ya cika wajen kuma ya fara raguwa sai tsamin giyar burkutu da ya maye gurbin warin gum kai kace a tsakiyar gidan Madam Saly -fara ake . Umarni yayiwa wasu bayi biyu da su ɗauke su su fita da su su riƙe . Jin haka yasa Hajiya Mama da tayi suman tsaye tun lokacin da ƙwaryar ta fashe cikin wani irin sauti mai faɗi fashe da matsanancin kuka tana duban jikin ta cikin tashin hankali da wasu zuƙa-zuƙan tsutsotsi da suke yama-yama a cikin ruwan suka hau jikin ta . Ihu ta sake kurmawa lokaci guda ta fara cewa "ku bani ruwa dan Allah kar su shige min cikin jiki wayyo Allah na shiga uku , Youssoufa Allah shi tsine maka ɗan bala'i . Jikin sa yana mazari ya taho gaban ta ya tsaya yana gyara riƙon bindigar sa yace "ina Mata ta ? "Ina kin ka kai min Mata ta ? "Ina Mata ta nake tambayar ki ? Bangaje shi Hajiya Mama tayi cikin yanayin da yake nuna ta daina fahimtar kome da gudu ta nufi hanyar fita mutane suka dare a tsorace suka buɗa mata hanya ta fita a guje . Wani irin duka Youssouf ya shiga kaiwa bango da hannun sa yana wani irin huci gaba ɗaya jijiyoyin jikin sa sun miƙe yana wani irin tsuma da duk ya tsorata mutanen wajen . Nan take hawaye ya fara sauƙa a fuskar Hajiya Umma . Maimartaba ne ya tako a hankali ya dafa kafaɗun sa kafin ya zarce da riƙe hannun sa da har ya fara fitar da jini . "Innalillahi wa inna ilahi raji'oon ,Lahaula wala kuwata illah billah huwal aliel azim ya fara maimaita masa cikin nutsuwa kafin ya kai hannu ya zare bindigar da yake riƙe da ita a ɗayan hannun sa . Wani irin kuka ya fashe da shi yana damƙe hannun Maimartaba da yake cikin nasa yace " Baba me na mata ? Meyasa ta min hakka ? Itta ta ɓata min rayuwa ta tayi sanadin da suna na ya ɓaci ƙima ta ta zubbe , iyayena sun ka yi fushi da ni , Baba me na mata ? " Ka ƙira ta ta dawo ta faɗi inda ta kai Mata ta , Ita tayi enlevé na Fatima " Me Fatima ta mata zata badda ta ? Ina ta kai Fatima ? Ya ƙara cewa haka da wata irin buɗaɗɗiyar muryar da tayi amsa kuwwa a baki ɗayan sashin . Falmata da take tsakiya da yin kuka cikin tsoron ko Hajiya Mama ta turo mata Aljannu ne su kashe ta kamar yadda ta faɗa mata a yanzu? domin da ta shigo ta ji tana karatun Alkur'ani . Shine ta mammake Mata baki ta ɗora da tsorata ta da cewa zata mata turen ifiritai su zuƙe jinin ta muddin ta sake karatun kur'ani . Jin tashin muryar Youssouf yana ƙiran sunan ta ya sa ta zabura ta miƙe zafin da ya ratsa ƙafar ta ya sa ta saurin komawa ta zauna wasu sabbin hawaye na sake zubo mata . Da rarrafe ta ƙarasa bakin ƙofar ɗakin ta soma bubbugawa da ƙarfi tana ƙiran sunan Youssouf . Da gudu Youssouf ɗin ya fito saboda shirun da wajen ya ɗauka ya bashi damar jin muryar ta a kusa . Duka ɗaya ya yiwa ƙofar ta karye da ƙiris ya rage bai faɗa mata akai ba . Yana shiga ɗakin ya zube guiwowin sa a ƙasa ya ɗago ta "Fatima-Zahra Est-ce que ça va? Alhamdulillah , Alhamdulillah ' Wani irin kuka ta fashe da shi tana ƙan-ƙame shi kamar zata koma jikin sa cikin kuka ta fara cewa " Dan Allah ka fitar da ni anan ka mayar da ni gida wajen Mamana, waccan matar ita ce ta kawo ni nan ta kulle ni yau kwana huɗu tace min zata kashe ni ,idan na yarda nayi magana , kai ma ita ta yi ma asiri kai da Yakaka ita tayi , ita tayi muguwa ce bata da kirki .... Jijjiga ta yayi da sigar rarrashi yace "va bien mon amour Votre protégé en toute sécurité maintenant babu abunda zatta sake iya yi miki kin ji Fatima ki nutsu ki daina kuka ? Tayi miki ciwo ? Ina yake miki ciwo ? Ya furta hakan yana ɗaga kallon sa zuwa kan Maimartaba da Hajiya Umma waɗan da suke ganin kome kamar a shirin film wai Hajiya Saratu da suke rayuwa da ita shekara da shekaru ita ce ta yiwa ɗan su duk wannan mugun ƙullin ?. Ko Hajiya Umma bata taɓa zaton sharri da muguntar Hajiya Saratu , bayan irin mummunan asirin da ta yiwa ɗan ta har ya kai da zata iya enlevé surukar ta ?? Wacce irin ƙiyayya ce wannan Hajiya Mama take mata ? Da hannu Hajiya Umma ta ƙira Ubbo da Siyama waɗan da suma suke tsaye kasaƙe kamar ruwa ya cinye su tace " ku kama ta zouwa sashi na . Cikin sauri Youssouf ya girgiza kai kafin yace " zan tai da ita da kaina. Gyaran murya Maimartaba yayi kafin yace " bar su su tai da ita kai kouma ka biyo ni . Daga haka ya juya bayu da sauran al'ummar gidan da har kawo yanzu babu wanda ya iya cewa ƙala wasu suka rufa masa baya . Youssouf bai saki hannun Falmata ba duk da cewa tun da ta ji muryoyin mutane a wajen ta raba jikin ta daga na shi amma ya ƙi sakin hannun ta . Har Sai da Hajiya Umma ta kama hannun Falmatan ɗaya ta rike sannan tace masa " ka tai ga ƙiran Mahaifin ka , itta tana ƙarƙashin kulawata . A hankali ya miƙe yana waiwayen Falmata da ta sunkuyar da kan ta ya fita zuciyar sa cike da jin tausayin falmata da ya lura har rama tayi ta fita a kamannin ta duk wai a sanadin sa Hajiya Saratu ta mata haka ? Ubbo da kan ta ta haɗawa Falmata ruwan wanka kamar yadda Hajiya Umma ta umarce ta , Hajja wacce yau ta samu damar shiga har uwar ɗakin Hajiya Umma tana sharar hawaye tace " mu je na gasa miki ƙafar ta ki uwarɗakina ko kya ɗan ji daɗin ta sannu kin ji Allah ya miki sakayya . Hajiya Umma da take kallon Falmata cike da tausayi cikin ran ta wani irin yanayi take ji zuwa yanzu ta fara yarda da cewa kamar da sakacin ta har Hajiya Mama tayi nasarar kama Falmata yarinyar da zuwa yanzu ta fahimci da ita da danginta baki ɗaya basu da wata alaƙa da halin da rayuwar ɗan ta ya kasance a ciki kamar yadda take zato a baya , ashe Hajiya Mama ita ce mafarin kome ba Falmata da 'yar uwar ta ba . Fuskar ta bata ɓoye halin da zuciyar ta ke ciki ba tace " kar a taɓa mata ƙafar za'a ƙira mai gyara yazo ya duba idan ma kuma asibiti za'a kai ta sai a tafi . Ɗan lankwasa kai Hajja tayi tace "to bari a jira , O' ni hauwa'u yau na ga kura da fatar akuya ganin idona , wasu mutanen launin hankaka ne da su gaban su fari bayan su baƙi ai ba ƙaramin marar imani bane zai yi kinnafin ɗin ɗan adam ba , yo ai tazarar da take tsakanin kinnafaa da boko haram kaɗan ce , Allah ya raba mu da miyagun mutane . A hankali Hajiya Umma ta amsa da "Amin dai , tana mayar da kallon ta kan Hajja. A can ɗakin ganawa ta musamman Maimartaba tare da manyan mutanen Fada nasiha suka dunga yiwa Biyamuradi Youssouf suna tausar zuciyar sa , sun gwada masa girman haƙuri tare da matsayin da mutanen da Allah ya yiwa baiwa da haƙuri suke shi tare a gurin sa da kusanci da haƙuri ke kawo wa tsakanin Mutum da Mahalccin sa Sannan suka jawo masa ayoyi da hadisai . A ƙarshe suka bashi tabbaci kan cewa jarabawar Rayuwa ce Allah ya masa domin ya gwada ƙarfin imanin sa dan haka ya bar kome ga Ubangiji da idanun sa zai ga sakayya . A hankali ya dunga jin nutsuwa na safko masa da kafin wani lokaci ya ji baki ɗaya zuciyar sa ta sauƙa wani irin nutsuwar da ya jima bai ji irin ta ba tana safko masa . Liman da yake malami masanin Alkur'ani ya cigaba da cewa "sannan shi sihiri gaskiya ne da masu aikata shi kaɗai suka yi imani da shi , "babu shakka cikin kur'ani duk wani magani da warakar kowacce cuta yake dan haka ga ayoyin Alkur'ani masu warware sihiri zan faɗa maka idan za ka iya kayi da kan ka Yousssouf idan kuma ka gaza ka bayar a yi maka ina mai tabbatar maka da cewa dukkanin wani sihiri da anka maka sai ya karye da iznin Allah sannan kuma Allah zai baka kariya daga dukkanin wani mgunta da za'a sake nufar ka da shi ta hanyar sihiri ba zai yi tasiri akan ka ba, ka samu takarda da alƙalami ka rubuta a yanzu Youssoufa ayoyin sune kamar haka : 1). Ta'awwizi da Basmala. 2). Fatiha kafa 7. 3). Aya biyar Ta farkon Suratul Bakara sau 7. 4). Ayoyi biyu ta tsakiyan suratul Bakara wato - Wa ilahukum ilahum wahid la'ilaha illa huwa har karshe sau 7. 5). Ayatul kursiyyu Suratul Bakara aya ta 255 sau 7. 6). Ayoyi uku a karshen Suratul Bakara wato daga baikin Amanarrasul Bakara 284-286 sau 7. 7). Shahidallahu a chikin Al Imran aya ta 18 da 19 sau 7. 8). Inna Rabbakumullahi Ladhi khalaqas samawati wal ardh.. acikin Suratul Al'araf aya ta 54 da 56 sau 7. 9). Afa hasibtum Annama khalaqanakum Abasan suratl Mu'minin aya ta 115 da 118 sau 7. 10). Wa Annahu ta'ala Jaddu rabbina mattakhadha..." a cikin Suratul Jinni aya ta 3 zuwa ta 9 shima kafa 7. 11). Aya goma na farkon Suratul Saffat shima sau 7. 12). Aya Uku na karshen Suratul Hashri wato "Lau anzalna hathal Quran. 13). Aya ta 10 na karshen suratul Yasin su ma sau 7. 14). Kulya ayyuhal kafirun sau 7. 15). Qul huwallahu ahad sau 7. 16). Falaqi sau 7. 17). Nasi sau 7. A rika tofawa a ruwan zamzam ko ruwan sama ko ayi a duka biyun amma dabam dabam a samo ganyen magarya a dandaka guda bakwai-bakwai har gida 7 wato na kwana 7 Safiya da maraice ana sha ana shafe jiki dashi. Da fatan ka Fahimta Yossoufa ? Sannan a kome kake kada kayi wassa da ibadar ka domin itta ɗin kariya ce mai girma daga dukkanin abun ƙi , ka faɗaɗa ibarda ka yalwata ta , sannan ka yawaita sadakha domin ita ma kariya ce .' Youssouf da yake gama rubutu ya ɗago kan sa fuskar sa a nutse yace" na fahimta Malam kuma Nagode Allah shi saka da alkhairi . Daganan ya baro sashin maimartaba bayan ya musu godiya mai tarin yawa , ya bar su suna cigaba da tattunawa . Sashin sa ya nufa kai tsaye yayi wanka ya ɗaura alwalar sallar la'asar zuciyar sa da take cike da tausayin Falmata da son sanin halin da take ciki ta sa shi dole ya miƙa hanya zuwa sashin Hajiya Umma . A zaune ya tarar da Hajiya Umma , a falon ta na ciki da Hajja sai kuma Ubbo suna sake jimamin lamarin banda ɓarin nauyayan kalmomi babu abun da Hajja take yi da lokaci-lokaci ubbo kan yi dariyar wasu kalmomin na Hajja . Zuciyar Hajiya Umma ta sanyaya da ganin Yousouf ya dawo cikin nutsuwar sa har ma ta gagara ɓoye jin dadin ta . Tayi hamdalah a bayyane . Bayan sun gaisa ta ɗan dube shi kafin tace " ƙafar Fatima da akwai ciwo domin kouwa da kyar take iya takawa duk da dai na mata tambayoyi cikin amsar da ta bayar tacce bata da wata damuwa sai ta ƙafar da daman akwai tsohon targaɗe a gurin kuma ta sake gurɗewa dan haka nayi magana a ƙira mai gyara a duba ƙafar ko kuwa asibiti za'a ? Cike da jin daɗin kulawar da ta nuna a karon farko ga Falmata , Youssouf yace "duk wanda kin ka ga yafi dacewa Umma. "Ka shiga ciki ka gan ta suna ɗaki tare da Siyama. A bisa ɗaya daga cikin gadajen Hajiya Umma biyu da suke ɗakin ya hango ta a zaune tayi wankan ta fes jikin ta sanye da doguwar riga ta atamfa daga gefe Siyama ce a kusa da ita hannun ta riƙe da wani ɗan kyakkyawan tasa ( Bowl ) da aka zuba ferfesun ƙaza a ciki da chokala biyu a ciki fork da soup spoons, Ganin shigowar sa bai sa Siyama ta fasa kai soup spoon ɗin da ta cika da ruwan ferfesun bakin Falmata ba sai dai ta amsa sallamar sa da murmushi akan fuskar ta . Ƙarasowa bakin gadon Youssouf yayi ya zauna a ɗaya gefen yana bin ƙafar Falmata da kallo wanda ta kumbura daga idon sawun . Kallon sa ya mayar ga Siyama yana jifatan ta da ɗan kyakkyawan murmushi yace "Siyama kina gatata ƙamnar ki hakka ? Da har kin ka ciyar da ita ba tare da ni kin tuna da cikina ba ? Ɗan murmushi Siyama tayi kafin tace " ai itta a yanzu marar lafiya ce kai kouwa ka samu waraka insha Allah . Murmushi yayi yana mayar da ganin sa kan Falmata yace "Fatima yaya ƙarfin jiki ? Ina ke miki ciwo bayan sawun ki ? Cikin 'yar ƙaramar murya tace "ba ko'ina sai ƙafar tawa. Tashi yayi daga bakin gadon ya ɗan yi durƙuso kafin ya kama ƙafar falmata a hankali ya ɗago ta , Ganin haka yasa Siyama tayi saurin miƙewa bayan ta ajiye kwanon hannun ta akan ɗan teburin gefen gado (bedside cabinet) . Ta nufi ficewa daga ɗakin " Maman Yumna ina za ki tai ? Youssouf ya furta haka yana bin ta da kallo Lumshe idanun ta tayi ba tare da ta jiyo ba tace " zan tai na kawo ma abinci . Daga haka ta ƙarasa barin ɗakin tana jin yadda suke kokawa tsakanin ta da zuciyar ta da take son ganin baƙin Youssouf da Falmatan. A hankali ya mayar da ganin sa kan ƙafar Falmatan ya kai ɗan yatsan sa babba ya shafa gurin da ya ɗan kumbura a hankali da yasa Falmata rufe idanun ta a hankali tana jin yadda tsiƙar jikin ta ke tashi tare da wani yanayi da take ji na tausayi mai girma yana huda zuciyar ta , yana bin duk wani saƙo da lungu da ɓurɓushin jin haushin Youssoufa ya maƙale a ran ta kan laifin da take zaton duk yayi su a bisa son rai cikin sanin sa da yin kan sa . Ji tayi laifukan sa na gogewa suna shafewa , ƙaunar sa , son sa , tare da tarin tausayin sa masu nawin da bata taɓa jin makamancin su ba saboda ji da tayi kamar zuciyar ta ba zata iya ɗauka ba , kamar sararin dake ran ta yayi kaɗan. da wani irin tasiri mai girma suke maye gurbin duk wani ɗan taƙi da ta bar wa soyayya mallaki a cikin ran ta . Tasirin so da take ji a lokacin ya fi ƙarfin rarraunar zuciyar ta da take sabon shiga a fagen soyayya . Ɗago da kan sa yayi yana kallon ta bayan ya gama tofa mata addu'o'i a ƙafar ta . Ya ɗan dau lokaci yana kallon ƙaramar fuskar ta da take sake zama 'yar firat yana jin tausayi tare da wannan son nata mai yawa yana masa yawo a zuci . Jin sa shiru ya sa ta buɗe idanun ta a hankali suka haɗa ido . "Sannu Fatima insha Allah za ki samu sauƙi kin ji kou ? Gyaɗa kan ta tayi A hankali ya miƙe ya ƙarasa ya ɗauki bowl ɗin da Siyama ta ajiye ya dawo ya zauna , ya fara bata ferfesun tana ci a hankali , har sai da ta ɗan ci dayawa kafin tace masa "ta ƙoshi . Bayan ya ajiye kwanon ya dawo ya zauna tare da riƙo hannun ta ya sarƙe 'yan yatsun su waje ɗaya "Fatima kiyi haƙuri da abunda ya same ki Allah zai miki sakayya cikin gaugawa kuma insha Allah zan zamar miki garkuwar da babu wanda shi issa ya taɓa ki a rayuwa na ƙyale shi , kiyi haƙuri Fatima . Matsa hannun sa da yake cikin nata tayi kafin ta ɗago kan ta tana saka idanun ta cikin nashi tace " Meyasa bata son ka haka ? "Nima ban sani ba Fatima cikin rayuwata ban taɓa yi mata laifi ba amma ta zuba min ƙiyayya mai zafi da har da taimakon ta anka nemi raba ni da raina bayan ita ta gurgunta rayuwata ta rarraba ƙiyayyar da take min tsakanina da ɗiyan ta da suke 'yan ouwana . Kan ta ta mayar ta kwantar a ƙafaɗar sa tana kaucewa kallon cikin idanun sa da suka fara sauya launi tace "Kayi haƙuri ƙiyayyar ta ba za ta sa ko ta hana kome ba sai fa abunda Allah ya rataya alhakin faruwar sa akan ta . "Idan ita bata son ka Allah da Manzon Allah su na son ka , Maimartaba yana son ka , Umma tana son ka sauran 'yan uwanka suna son ka , Siyama tana son ka , yaran ka ma zasu so ka . Ɗan jim tayi kafin ta ɗago kan ta tana kallon cikin idanun sa tace " kuma ni ma ina son ka , Ina son ka , ina son ka dayawa . A bazata ya tsinkayi kalmomin da bata taɓa furta masa ba , zuciyar sa tayi wani ɗan ƙaramin zillo da yasa shi sake ɗago fuskar ta da sauri ya riƙe ta yana kallon ƙwarar idanun ta , muryar sa a tsakani maƙoshin sa yace "me kika faɗi Fatima sake faɗi naji ? Maimaita min ? "Ina son ka dayawa dayawa ba adadi Ta sake furta hakan tana kallon fuskar sa cikin ranta " godiya take yiwa Ubangiji da idan ba shi ba da ƙarfin ikon sa wa ya isa mallaka mata wannan mutumin ma'abocin kyau da cikar zati tare da kyaun nasaba ? Muryar sa tana sake nitsewa saboda ƙasa da yayi da ita yace "dagaske Fatima ? Hannuwan ta tasa akan nasa kafin tace "da duk gaskiyar zuciyata ina son ka dayawa , Wani irin sanyi yake ji tun daga ƙasan ran sa yana taso masa yana nitsar da idanun sa cikin nata yace " son da nake miki yafi wanda kike min yawa Fatima , son da nake miki ba shi da iyaka , ni ban san iyakar sa ba, kin yarda na gwada miki ɗigo dagga cikin sa ? Kan ta ta gyaɗa masa tana murmushin da yake bayyana haƙoranta , Tazarar dake tsakanin su ya haɗe yana manne fuskar sa da ta ta , tare da shauƙin son da suke yiwa junan su suka himmantu wajen gwadawa junan su tatatciyar soyayyar da suke yiwa juna . Ƙwanƙwasa ƙofar da Aka yi yasa su sa rabuwa da jikin juna , Ba'a jinkirta ba aka murɗo ƙofar a hankali ta shigo bakin ta ɗauke da Sallama . Siyama ce ta shaida musu zuwan mai gyaran ƙafa . Yousaouf ya masa iznin shigowa bayan ya gyara mata mayafi. Ba ƙaramar azaba Falmata ta sha ba kafin ƙashin da ya fita ya koma saboda tsamin da ƙafar tayi kwana huɗu da targaɗe . Siyama da Youssouf su suka dunga rige-rigen share mata hawaye da gumin da ta haɗa sharkaf duk kuwa da sanyin ɗakin . Bayan ta dawo cikin nutsuwar ta lokacin Youssouf ya bar ɗakin daga ita sai Hajja da ƙaramar murya ta cewa Hajja " Hajja ki bani wayar ki zan ƙira Mamana da Yakaka . Ɗan jim Hajja tayi kafin da sigar rarrashi tace "Uwarɗakina Amma fa kar ki shaida musu abunda ya faru da ke domin ba'a sanar da su ba tun da Allah yasa kin fita lafiya kar ki faɗa musu kuma zuciyar su ta kasa nutsuwa da zaman ki anan . "Ba zan faɗa musu ba Hajja kawai so nake naji muryar su mu gaisa . "To babu laifi ga wayar ki ƙira su . Sun jima suna Hira da ita da iyayen ta Khaalty Rahima da Amnee inda har suka yi ƙorafin cikin kwana biyun sun yi ta ƙiran layin Hajja bata ɗauka musamman ma a jiya da Yakaka ta koma Abuja . Cikin ɗoki Falmata take sake tambayar su 'Yakaka ta tafi gidan ta ? Amnee ta bata amsa tana dariya da cewa "jiya suka tafi tare da yayan naku takwarata an zama 'yan Abuja ( kamar Ammi Haseen 🤣) Cikin zaƙuwa Falmata ta fara ƙiran layin Yakaka bayan sun yi Sallama da su Amnee. Sai dai ƙira biyu tayi ba'a ɗauka ba , yamutsa fuska tayi tana sake danna ƙiran take mitar " Yakaka ko ina ta ajiye wayar ??? ABUJA NIGERIA Kai-kawo Yakaka ta cigaba da yi a cikin banɗakin da take tsaye , karo na barkatai ta sake sunkuyawa tana leƙe ta ƙafar ɗan makulli , da sauri tayi baya tana sakin wani ƙaramin ihu ƙiris ya rage ta faɗi saboda santsi jikin ta na karkawa ta dafe ƙirjin ta tana mayar da numfashi . Idanun ta ba ƙarya suka mata ba tirƙeƙen karen da take hangowa tun safe a can nesa daga tsakiyar ɗakin wani lokaci kuma ta hango shi a gefe shine ta gan shi daf da ƙofar a yanzu kamar ma shima leƙen ta yake ta inda take leƙawa dan babu shakka sun yi ido huɗu ita da shi.. Zamewa tayi ta zauna a ƙasa dirshan cikin banɗakin daga inda take tana iya jin wayar ta dake ƙara lokaci zuwa lokaci tsawon yinin amma ba damar fitowa ta ɗau wayar saboda tirƙeƙen karen da yake ta shawagin sa a ɗakin har gado yake hawa yana sauƙa . A hankali ta saki wani sabon kukan da aƙalla tayi irin sa fiye da sau goma daga safe zuwa yanzu da ta tabbatar yamma tayi rana kuma tana gaf da faɗuwa . Assalamu Alaikum masu karatu da fatan kuna lafiya ? Yau dai bakina da goro ba zan ce kome ba bayan fatan alheri da nake muku a koyaushe. Nagode.[3/7, 3:55 PM] +234 706 503 6187: Mafari ( Hargitsin Rayuwa ) Umm'muaz 52 Ƙarar Turo ƙofar daƙin da Yakaka ta ji yasa ta tashi da sauri daga inda ta rakuɓe tana kuka ta zo jikin ƙofar ta ƙafar ɗan makulli ta leƙa . Sofi ta hango ta shigo, duk da halin firgicin da take ciki bai sa ta kasa ganin irin kwalliya ta ɗaukar magana tare da jaan hankalin duk wani ɗa namijin da ya ɗora idanun sa akan ta ba da Sofia tayi . Wani ɗan fito Sofi ta yiwa ɗirkeken karen nan ( Working dog ) sai ga shi ya dako tsalle daga kan gadon da Yakaka bata san yaushe ya haye ba , ya taho jikin ƙafafun Sofi yana kaɗa jela tare da sunsuna ta . Ƙaramar dariya Sofi tayi kafin ta ɗan yi sunkuyo ta shafa kan karen da farin ciki a sautin ta tace " oh Sam do you know how handsome you are ? You've got the best underbite, and the best butt muscles , Oh Sam I Love you , you really did a good job baby. Lokacin da ta ɗago kan ta wata ƙatuwar harara ta wurga a saitin ƙofar banɗakin kafin ta jaa wani dogon tsaki tana juyawa akan ƙafafun ta Sam ya bi bayan ta da ɗan gudun sa suka ƙarasa ficewa a ɗakin. Wata doguwar ajiyar zuciya Yakaka ta jaa tana dafe ƙirjin ta kafin ta ƙarasa zama a ƙasa tana jin wata 'Yar nutsuwa na safko mata, "Anty sofi Muguwa ce , ta aiyana hakan a cikin ran ta lokacin da ta tuno yadda tsakanin su yakasance a ɗazu da safe bayan fitar Doctor Hamza da yayi sammako ƙarfe shida na safe ya bar gida . Bayan fitar sa ta tashi tana son tattara ɗakin kafin ta fita gaishe da Sofi ta dawo ta hau gado ramuwar baccin gajiyar hanya da suka sha saboda a jiya basu iso gidan ba sai wajen ƙarfe sha biyu na dare dan haka ko da Matar gidan basu gaisa ba . Ƙarar turo ƙofar da aka yi yasa ta ɗago kan ta Sofi ta gani jikin ta da rigar baccin da take bayyana rashin kamun kan ta a sarari kan ta ko ɗan kwali babu , da sauri ta sunkuyar da kai tana janye ganin ta . Ta buɗe baki da nufin gaishe ta kalmomin ta suka ƙaƙare lokaci ɗaya numfashin ta ya shiga kai kawo yana ƙoƙarin fisgewa daga jikin ta lokacin da tayi ido huɗu da wani ƙaton mummmunan baƙin kare da ya taho yayi tsaye a bayan Sofi kamar ɗan matashin zaki . Kamar wacce aka soka da tsinin mashi ta tsala wani irin ihu lokaci ɗaya kamar mai fiffike ta hau saman gadon ta maƙure a ƙarshen gado ko'ina na jikin ta rawa yake yi . Da hannu ta shiga nunawa Sofia karen wacce tayi tsaye kiƙam tana kallon ta tashin hankalin da take ciki a lokacin ya hana ta fahimci yanayin da ke kan fuskar Sofi , ko kalma guda ta gagara fitowa daga maƙoshin ta sai da hannu take ta nuni tana wani irin takure jiki . Wata shashashar dariya Sofi tayi kafin tace "Ah Amarya ya da ihu da karkawa haka ? Sam ne fa ya zo yiwa sabuwar uwarɗakin sa sannu da zuwa. 'Sam . Sofia ta ƙira shi sai ga shi ya zagayo daga bayan ta ya tsaya tare da zubawa Yakaka jajayen idanun sa da yasa fitsari fara bin ƙafar ta . Wani ɗan guntun abu da har yanzu bata san mene ne ba , shi Sofia ta wurga mata a jiki da yasa karen yin wani irin tsalle sai ga shi akan ta yana buɗe haƙora . Daga lokacin bata san me ya kuma faruwa ba kawai sai farkawa tayi ta gan ta a ƙasa a yashe kusa da ƙofar banɗaki da ta miƙe zaune tana ƙoƙarin tuno abunda ya faru , tunanin nata bai je ko'ina ba haushin da karen ya yi yasa ta neman wajen tsira da ta faɗa cikin banɗaki ta rufe . A ciki ta ƙarasa tuno kome da ya faru kamar yadda ta gama yinin ranar a ciki , ba cin abinci , ruwa ma na banɗakin take tara daga fanfo ta sha . Tana sharar hawaye ta sake sunkuyawa ta leƙa sai da ta tabbatar babu kowa a ɗakin sannan ta buɗe ƙofar a hankali ta leƙo tana sake dube-dube . Da ta tabbatar babu kowa sai ta fito a hankali tana jin yadda jiri ke safko mata saboda mummunar yunwa da take ji rabon ta da abinci tun jiya a hanya da ta ɗan tattaɓa abincin da Doctor Hamza ya saya mata da ba wani na kirki ta saki jiki ta ci ba saboda 'yar kunyar nan ta Amare . Kai tsaye babbar jakar kayan ta ta nufa wanda ta zuba kayan ta masu amfani a ciki ta ɗau pad ta koma banɗakin ta gyara jikin ta , lokacin da ta fito bakin gado ta zauna ta rafka tagumi ɗakin da kan sa tsoro yake bata gefe guda kuma tana tsoron fita falon , ɗan kasa kunne tayi ta fara jin kamar muryar Doctor Hamza daga falon , tsam ta miƙe ta nufi ƙofar kai tsaye ta murɗa . Abun da ta hango ya sa tayi turus! Sofia ce a zaune ɗare-ɗare akan ƙafafun doctor Hamza tana iya hango haɗuwar fuskokin su daga inda take tsaye , cikin sauri ta janye ganin ta daga kansu saboda a lokacin ita yunwar da take ji yafi kome damun ta musamman da yakasance tana Menstruation period dan haka wata irin gigitattar yunwa take ji . Da dabara Doctor Hamza ya janye fuskar sa daga ta Sofi wacce tun yana sanya ƙafa cikin falon ta bi ta kanainaye shi da kissa ta katse masa hanzari da zumuɗin da ya shigo da shi na son ya isa ga Yakaka . da tsawon yinin duk ya yi cikin kewar ta da son sanin halin da take ciki musamman ma dai da ya dunga ƙiran wayar ta bata ɗauka , hankalin sa tashi yayi, sai da ya ƙira Sofi ta ba shi tabbacin lafiyar ta ƙalau kawai baccin gajiya take yi duk da dai yayi mamaki amma ya samu nutsuwar zuci . Sannan kuma ya ji daɗin jin muryar Sofi cike da kwanciyar hankali da raha ba kamar yadda yayi zato ba da har yake jin shakkun barin su a tare . "Sofi kyale ni haka nan duk a gajiye nake jikina ma duk ciwo yake min ke kuma kin zo kin sake ɗora min nawin waɗannan kayan naki . Ya ƙarasa faɗin hakan yana ɗan dukan bayan ta cike da tsokana . Matsar da fuskar ta sofi tayi tana wani ɗan mitsitsin murmushi . Karaf idanun sa suka sauƙa kan Yakaka wacce take ta raragefe ta bayan kujeru cike da tsoron sake ganin karen nan take neman ƙofar kitchen . Ware idanun yayi kafin ya ƙira ta "Wafaa . Sofi bata ankara ba ta ji ya tunkuɗe ta gefe ya miƙe da ɗan sauri ya isa ga Yakaka wacce idanun ta da suka yi zuru-zuru suke bayyana halin ruɗani da tsoron da zuciyar ta ke ciki . "Wafaa , me ya same ki ? Yakaka wacce ta ɗan sake jaan baya , tana ƙin haɗa ido da shi kan ta a sunkuye tace "Yaya Dacta yunwa nake ci tun safe ban ci kome ba . Kafin ya buɗe baki Sofi wacce har ta baro inda take a ɓingire ta gyagije tayi wuf tace "Ah Amaryar Ya-ka-ka har an gama baccin asarar an tashi ? To ke kuwa kya fito haka ? Dagaje-dagaje ? Yarkace-yarkace fuska duk yawun bacci kina Amarya.... Da hannu Doctor Hamza ya dakatar da ita , "Sofi ina Abincin ta ? A Bata ta ci yunwa take ji... Wani irin kallon sheƙeƙe Sofi ta masa tana ƙanƙantar da ido ta ɗaga yar mitsitsiyar rigar ta ɗan shafal ɗin cikin ta da manyan cinyoyin ta suka sake shanye shi ciki ya bayyana . "Doctor ka ga fa nima nawa cikin haka yake empty ba kome ka dai san bana jurar shiga kitchen na girkawa kaina ma bare wannan gantsareriyar . Bai saurare ta ba ya matsa da sauri ya taro Yakaka da take ƙoƙarin durƙusawa saboda duhu-duhu da take gani. "Wafaa duk yunwar ce ? Sannu muje ki shirya sai mu tafi mu ci abinci kin ji ? Da sauri Yakaka ta zamewa riƙon da yayi mata tana jin nawin kar hancin sa ya shaƙo wani mummunan yanayin da bai dace ba daga jikin ta duk kuwa da tasan ƙamshi irin nasu na gado ya zauna mata a sassan jiki amma ai jikin ɗan adam ruwa ne . "Yaa Dacta a nuna min kitchen ɗin jiya Amnee ta min miya na taho da ita sai na ɗumama na dafa mana wani abu mu ci da sauri ba ma sai an tafi wajen sayar da abinci ba ' Sofi wacce ta shaƙa har wuya sai cewa tayi "ɗumame za ki mana da daren nan ? "Za ki iya Wafaa ? Yace yana ɗago haɓar ta da ɗan yatsan sa , da son ganin ƙwarar idanun ta "Zan iya Ya dakta , tace tana zame fuskar ta "To muje na nuna miki. Kyale ta zan nuna mata kai muje kayi wanka Doctor kayi shirin Magarib tunda ta gabato kai da baka yarda jam'i ya wuce ka ' Har zai ce wani abu sai kuma ya fasa yana ɗaukar briefcase yace "ki taya kuyi please jikin ta ba ƙarfi sosai . Wani mugun Kallo Sofi ta bi shi da shi kafin ta dawo da ganin ta kan Yakaka da tayi ƙulus tana jiran ta. "Muje Ta ce tana yin gaba hannu dama suka bi sai ga su a cikin ɗan wani Straight kitchen da bai cika girma ba. Suna shiga Sofi ta hankaɗa Yakaka , ƙiris ya rage ta ci karo da cabinet. ta matsa gaban ta tana rangaji cikin irin takun ta , muryar ta cike da kaushi tace "Barkan ki da shigowa cikin rayuwata , ina yi miki barka da shigowa cikin gona ta , ban iyakance miki iyakar adadin nau'ikan azabar da nake kan yi miki tanadin su ba na dai san babu shakka za ki iya zaɓar mutuwa ta hanyar rataya akan rayuwar da za kiyi a gidana . Idanun ta da suka yi jawur Sofi ta tsare ta da su da suke tabbatarwa da Yakaka sahihancin zantukan da ta furta kafin ta cigaba da cewa "Kuskure mafi girma da kika yi shine auren Mijina , tsautsayi da ya hau kan ki kuma har kika tako kafafun ki cikin gida na da zummar yin rayuwar aure da Mijina , yaudarar kai ta sa ki tunanin samun kwanciyar hankali a rayuwar gidana , wuce iyakar da zai kai ki ga faɗawa cikin bala'i Mai girma shine ki haɗa shimfiɗa da Mijina . Guntu murmushi sofi tayi kafin ta ɗora da cigaba da cewa " wautar da za kiyi kuwa ita ce ƙoƙarin shiga tsakanina da Mijina ko kuwa nace ki nemi kai ƙara ta anan za ki ga ainahin launi zuciya ta da ta ɓoyu cikin bayyanannar fuskata . Juyawa tayi ta ɗau wata wuƙa kakkaifa daga cikin jerin wuƙaƙen ta da suke block a jere ta juya tsinin wuƙar saitin Yakaka wacce take tsaye kamar mutum-mutumi . "Kin ga wannan wuƙar ita zan saka na farka cikin ki duk ranar da kika yi kuskuren sakarwa Mijina jiki har ta kai ki ga ba shi wannan busasshen jikin naki Marar maiƙo banda ma jarabar namiji me zai ci a wannan wajen ? ta ƙarasa zancen tana nuna ƙirjin Yakaka da tsinin wuka . "Wafaa . Sautin Doctor Hamza ya ratso wajen daga bayan su hannun sa riƙe da wani ɗan babban cup da chokali a cikin sa yana juya tea mai kauri da ya haɗa . Jallabiyar jikin sa bata boye sauran danshin ruwan da yayi wanka da shi ba , ya ƙaraso cikin kitchen ɗin lokacin da Sofi take ajiye wuƙar a gefe ta juyo da murmushi a fuskar ta tace " kar ki manta da abunda na faɗa miki ki kiyaye Bari nima nayi Sallah . Bata dubi Doctor Hamza ba ta bar kitchen ɗin saboda zuwa lokacin kishin ta ya fara kaiwa matakin da ya wuce kissa ta ɓoye shi , zuciyar ta ba zata juri ganin Hamzan ta yana ko da yiwa wata mace magana bane bare bata kulawa kuma ma wai a matsayin matar sa ita ganin ƙoƙarin kan ta ma take yi da bata fara yunƙurin kashe Yakaka ba , ko da yake Samira ce take hana ta a cewar ta kissa da kisisina kaɗai ya ishi Yakaka . Bayan fitar ta Dactor Hamza ya matso kusa da Yakaka wacce har lokacin kalaman Sofi ke mata yawo a kunne suna ɗarsa mata wani mugun tsoro a cikin ran ta . Sanyin hannun sa ta ji a cikin nata ya sa tayi firgit tana zame hannun ta , bai bata dama ba ya riƙo hannun ta ya jaa ta zuwa kan standard-chair bayan ya ajiye tea ɗin ya taimaka mata ta zauna. Ɗaukar tea ɗin yayi ya kurɓa ya ji ɗumin sa yayi dai-dai ɗumama ciki. Dan haka ya kai kofin bakin ta a hankali muryar sa a ɗan ƙasa yace "ki shanye zai taimaka wajen dawo miki da kuzari bayan ya rage miki yunwa . Hannun ta ta kai zata karɓi kofin , amma sai ya janye ya hana ta , da hannun sa ya sake kusanta kofin da bakin ta . Ba yadda ta iya haka ta buɗe baki ya fara bata , har sai da ta shanye A take gumi ya tsattsafo a goshin ta ta sanya bayan hannun ta da ya sha jan ƙunshi da aka mata tsararren zane da ya zanu akan farar fatar ta tare da ƙara fiddo zallar kyaun zara-zaran yantsun hannun ta masu tsini , ta goge gumin kan ta ɗauke hannun ta taji sassanyan hannun sa yana taya ta . Ganin haka ya sa ta fara ƙoƙarin miƙewa amma sai ya sake matso ta ya hana ta tashi , a hankali ta ɗago kai tana kallon fuskar sa cikin sa'a idanun su suka haɗu wani yanayin da ta gaza jurewa a cikin idanun sa take hangowa dan haka tayi saurin sunkuyar da kai . "Meyasa kika ta yin bacci haka kika zauna da yunwa ? Bakyau zama da yunwa kin ji ? Nan gaba kar ki sake bacci mai yawa haka da rana , an fison mutum yayi irin wannan baccin da dare kin ji ko wafaa ? So take ta ce ba bacci tayi ba so take ta faɗi ainahin abinda ya faru sai dai rarraunar zuciyar ta da take maƙare da tsoron Sofi tana tunasar da ita kalaman Sofi tare da sake faɗa mata makomar ƙaryata Sofi da zata yi muddin ta fadi gaskiya . "Wafaa. ya sake ƙiran sunan ta "Unm ta amsa . "Ki daina min shiru-shirun nan ki dunga amsawa idan na miki magana kin ji ko ? " To Yaya Dacta bazan sake ba. Goshin ta ya sumbata a hankali kafin yace "Ni zan je masallaci na dawo Miyar da muka taho da ita jiyan tana fridge kin ji ? A hankali ta gyaɗa kai . Ya juya yana barin kitchen ɗin , kafin ya ƙarasa falo Sofi ta bar gurin da take laɓe da gudu ta hau sama ɗakin ta . A gurguje Yakaka ta tafasa shinkafa ta nuna ta tsantsame ta juye a warmer ta ɗauko miyar bayan ta juye a wata tukunyar ta daban ta ɗora ta tana fara dumamuwa ƙamshi ya ɗume gidan . Kafin wani lokaci ta dumamu ta zuba miyar a wata warmer da bata kai waccan girma ba , So take ta koma ɗaki ta yi wanka ta kintsa jikin ta amma tsoron haɗuwa da Sofi ya hana ta fita , dan haka tayi zaune kawai a kitchen ɗin. Idanun ta ya sauƙa kan babbar jakar bacco da suka taho da ita a jiyan wanda kayan kamsasa girke-girke ne a ciki da kuma na shayi wanda Amnee ta haɗa mata su tana sake jaddada mata amfanin su sosai da sosai . Ganin tana zaune kawai sai ta sake miƙewa ta haɗa ruwa a tukunya bayan ta zuba haɗin kayan shayi wanda Amnee ta nuna mata su dalla-dallah dan haka ta ɗau wanda ta nuna mata shine na dare saboda cikin ganyen akwai sinadarin wartsake gajiya , sugar kaɗan ta diɓa daga sugar-bowl ta zuba saboda shayin ma bai cika yawa ba kuma Amnee ta faɗa mata cikawa shayi sugar yana rage daɗin sa ya hana garɗin sinadaran da aka yi amfani da su fitowa . Daga lokacin da ta ɗora shayin zuwa mintoci biyar da suka biyo baya da fara tafasar shayin wani irin ƙamshi ne mai samar da nutsuwar zuci ya cika gidan har maƙota . Doctor Hamza da tun yana waje ya fara shaƙar ƙamshin da kai tsaye ya masa jagora zuwa kitchen daga bayan ta ya tsaya yana kallon ta lokacin da take juye shayin a wani stainless steal tea-set ƙirar Retro Titanium da Sofi ta saya a wani zuwa da tayi UK . Amma tunda ta kawo su sai dai koyaushe a goge su a ajiye ba'a taɓa amfani da su ba . A hankali ya tako ba tare da ta ji sautin takun sa ba sai ji tayi ya mata rumfa da ƙirjin sa da yasa ta saki wani ihun tsorata da tayi . Da sauri ya juyo da ita da hasken lantarki yake kallon ta , yana ɗan nazarin ta yace "Wafaa me ya tsorata ki haka ? Na lura tun zuwana a tsorace kike ko wani abu ya faru ? Girgiza kai tayi kafin ciki ƙaramar murya tace "Kai ka tsorata ni na ɗauka kare ne . "Kare kuma ? Yace da mamaki a muryar sa . Sake gyaɗa kai tayi alamar "eh " Wafaa bani da kare a gidan nan mai zai kawo kare ? Da sauri ta ɗago kan ta da son ran ta ne tace "akwai kare mana yau ma da shi muka wuni a ɗakin ka " Hannun sa da taji akan ƙirjin ta ya katse mata tunani da sauri ta ɗora hannun ta akan nashi idanun ta na fiffitowa ta fara kokawar janye hannun sa. "Shittt yace mata yana dauke hannun ta daga kan nashi ba tare da ya janye nasa hannun ba ya saurara kadan, kafin yace "Ki ji yadda zuciyar ki ke tsananta bugu ? Ba kyau saka tsoro haka a cikin rai yana da hatsari ga lafiya. Firgicin jin hannun sa a ƙirjin ta ya hana ta fahimci bayanin da yake mata. So take kawai ya ɗaga hannun sa , a hankali ya janye yana nazarin baƙon yanayin da ya bayyana a fuskar ta , ɗan murmushi yayi kafin yace . "Muje kiyi wanka ki shirya , Amarya sukutum ba kwalliya Wafaa ? Nayi zaton zan dawo na same ki kin min kwalliyar da zata mantar da ni duk wata guntuwar damuwa , oya muje kiyi wanka . Shi da kansa ya haɗa mata ruwan wanka kafin ya fito tayi shirin wanka bayan zanin da ta ɗaura ta zura dogon hijabin ta har ƙasa ta dawo bakin ƙofar banɗakin ta tsaya a ɗarare baki ɗayan ɗakin tsoro yake bata. Yana fitowa ya gan ta a tsaye da sigar tsokana yace "muje na miki ? Da sauri ta girgiza kai "zan yi da kaina. Har ta murɗa ƙofar ta shiga sai kuma ta dawo ba tare da ta yarda sun haɗa ido ba tace "Dan Allah ka jira ni kar ka fita . Gyaɗa kai yayi cikin ran sa ya fara mamakin tsoron ta yace "bazan fita ba kiyi wanka da kyau kin ji ? Ko da ta shiga banɗakin kasa rufe ƙofar tayi sai ta tura ta kawai . tana tsakiya da wanka ta ji kamar ya fita jikin ta duk kumfa ta matso bakin ƙofar " Yaya Dakta Ta ƙira suna sa da 'yar ƙaramar murya dan ta tabbatar yana nan. Shiru yayi bai amsa ba duk da cewa ya ji ta sai ya taso a hankali ya bar aikin da ya fara yi a laptop ɗin sa. Sake matsowa tayi tana buɗe ƙofar kaɗan ta ƙira sunan sa da ɗan ƙarfi dai-dai da ƙarasowar sa wajen . Karaf suka haɗa ido da shi . Salati ta sa tana yin baya da gudu ta rufo ƙofar tana jin wata matsananciyar kunya na neman sa ta kuka . "Shine kana jina ba zaka amsa ba wallahi ka bani tsoro meyasa za ka leƙo ni ina banɗaki ? Muryar sa tana bayyana dariyar da ta taho masa yace "ah leƙa ki nayi ? Ba ke kika ƙirani ba ? "To meyasa baka amsa ba kawai ? Ta furta hakan muryar ta a shagwaɓe da jin haushin sa . "Gani nayi zuwa da kai yafi saƙo , kuma ban sani ba ko ƙira na kike na wanke miki baya . Ya furta hakan lokacin da ya koma ya zauna har yanzu dariyar shirmen ta yake gefe guda wani irin nishaɗi ne yake ji yana ratsa shi . bayan ta gama wankan tana ƙudindine cikin Hijabi ta fito kai tsaye wajen da akwatin kayan ta yake ta nufa tana ƙin kallon sa . Bata wani bincika ba ta ɗau wata jar atamfar ta da take sama sabon ɗinki ne fil acikin kayan da Baaa ya mata . Banɗakin ta koma ta sanya kayan bayan ta ɗan shafa mai da ta gani a ajiye gaban makeup-mirror da yake banɗakin . Riga da siket ɗin da ta sa sun zauna mata ɗas a ɗan tsararren murmurarren dogon jikin ta da mazauna ƙasar Amurka ke kiran mata masu zubin jikin ta da Miss-champagne, Mutan ƙasar ingila kuwa suka ƙira ta da Miss-Magnificent. Lokacin da ta fito tana gyara ɗaurin ɗankwalin ta Doctor Hamza shagala yayi wajen kallon ta ya manta da abokin aikin sa da suke yin wata tattaunawa da shi a laptop. Gaba ɗaya kyaun ta ya ɗau hankalin sa kafin ƙamshin sassanyar haɗin Humra ya game masa hanci da ta buɗe cikin kayan ta ta ɗauko ɗaya daga cikin kwalaben da ta taho da su ta tsiyaya kaɗan a tafin hannu ta shafe jikin ta da shi . Yanayin ta na sanyi da nutsuwa shine yanayin da yafi so da ita komen ta sannu kan hankali take yi babu kwarafniya , irin ta irin matan da yake mafarkin samu kenan . Da ɗan murmushin da yake cikon halittar ta tace "Yaya Dakta nagama . Shiru ya ɗan yi yana kallon ta bai ƙi ba ace tayi tsaye haka nan gaban shi yayi ta kallon ta zuciyar sa na daɗa ƙawata masa kyaun halittar ta. Yamutsa fuska ta ɗanyi saboda ta fara siƙewa da yunwar da take ji , "Yunwa nake ji.. Kafin ta ƙarasa magana ya miƙe ya tako a hankali ya kama hannun ta suka fita tare "muje ki ci abinci Wafaa . Basu tarar da Sofi a falon ba , dan haka Doctor Hamza ya zaunar da ita akan ɗaya daga cikin kujerun falon yace "bari na ƙira Sofi kafin nan zuba mana abincin . Da ɗan saurin sa ya nufi sama , Sofi wacce daman tana laɓe daga sama jin tahowar sa yasa tayi sauri ta fito daga maɓoyar ta , Tayi wanka ta sake sabon shiri cikin wata evening gown backless, launin sararin samaniya da ta bi tsarin jikin ta irin na matan da suka ɗau duniyar su da faɗi suke bin dare da rana wajen ganin zubin jikin su ya koma haka watau (Wisdom tooth body). Rigar ta bi jikin ta ta lafe sassan jikin ta da suke da ɗaukar hankali sun bayyana a sarari. Jikin ta ta haɗa da nashi ta fara masa salo , da sauri ya riƙe hannun ta da ta ɗaura akan ƙirjin sa yana dawo da nutsuwar sa dai-dai yace "Sofia wannan kayan bai yi ba ki je ki sauya kin san dai ba mu kaɗai bane a gidan nan ? Bai dace ba ki fito a haka . Kaɗa ido tayi cike da shanye ruɗanin da ta shiga ganin yadda yau yake kawar da ido daga kan abubuwan da a da baya motsin kirki idan tana masa juyi a gaban sa tace "Doctor dan ka ƙaro aure ne zan kasa sakewa a gidannan ko meye ? It.... "Sofia pls ki fahimceni ko da a gaban mace 'yar uwar ki bai dace ki fita haka ba jikin ki duk a bayyane , kuma . Ɗan tsahirtawa yayi yana kallon yadda koɗaɗɗiyar fuskar ta ta fara yin jaa da bayyanar ɓacin rai , gudun rigamar ta yake yi sosai dan ya san mahaukacin kishin ta baya so yayi wani abu da zai sa ta ƙullaci Yakaka dan haka ya riƙo hannun ta yana sake tausasa murya yace "kuma ai kin san dai ina kishin ki sosai unh my pump truck ? Ɗan murmushi tayi tana jin zuciyar ta na farfaɗowa , haɗa jikin su ta sake yi tana kwantar da kan ta a kafadar sa a hankali tace "Doctor your Love is my strength and hope in this life always remember this. Ajiyar zuciya yayi baki ɗaya hankalin sa yana ga Yakaka ya ɗan ɗagata daga ƙafaɗar sa "Sofi kiyi sauri ki sauya kayan ki sauƙo mu ci abinci Wafaa tana jiran mu . Zamewa yake ƙoƙarin yi yaji ta riƙe hannun sa , cike da gajiya ya ɗaga idanun sa zuwa fuskar ta , hawaye ya gani sun ciccika gurbin matsakaitan idanun ta suna daf da fara sauƙa , "Sofia menene kuma ? Ya furta hakan cike da gundura . "Ka raka ni na chanja kayan sai ka zaɓar min wanda ya maka . Tausayin raunin da ya hango a tattare da ita da ya san son shi da tsananin kishin sa da take ya sa haka , sai ya gaza musa mata a ƙoƙarin sa na son kyautata mata ya rage mata raɗaɗin da take ji ya bi ta hannun su haɗe cikin na juna suka shiga ɗakin Sofi ta rufo ƙofar ta murɗa key . Yakaka baki ɗaya tayi laushi a zaune kan kujera tun kan ta na sunkuye tana jiran ta ji takun sauƙowar su har ta kai ta fara ɗaga kai tana kallon ƙafar benen . Ganin ko alamar su babu ita kuma yunwa na neman halaka ta yasa ta sauƙo.ƙasa gaban abincin ta zuba kaɗan a Plate ta cinye daɗin ɗanɗanon miyar Amnee da ta wadatu da kaji kamar zata tsinke mata kunne har wani lumshe ido take . Kafin ta farga ta cinye cikin zaƙuwa ta daɗa wani , a cikin nutsuwa take cin abincin ta bata ankara ba sai da ta cinye kusan rabin abincin ta ɗaura da ruwa taji cikin ta dam . Ta dawo nutsuwar ta sai lokacin ta fara farga da daɗewar da suka yi basu zo ba , ƙaton agogon falon da yake aiki ta duba ta ga har ƙarfe goma na dare saura 'yan mintoci . Shirun da duniyar baki ɗaya ta ɗauka a kunnen ta ya tafi ya tado da maƙallalen tsoron da yunwa ta binne shi , Ɗas!Ɗas! Ƙirjin ta ya buga da tuno ƙaton karen da ta tabbata yana nan a cikin gidan yana shawagi . Sauƙa tayi daga kan kujerar ta takure a ƙasa tana jin yadda baki ɗayan tsikar jikin ta ke miƙewa ' Tsoron ta yana sake hauhawa da ƙaruwar kowacce daƙiƙa ɗaya , bata san lokacin da ta miƙe ba a hankali ta nufi ƙafar benen ,sai kuma ta jaa ta tsaya tana jin shakkun hawa sanin da tayi ɗakin Sofi ne a saman , ita tsoro take ji sun bar ta ita kaɗai ko da ba zasu yi hira ba su sauƙo ta dunga ganin su . Muryar ta tana ɗan rawa tace "Yaya Dacta , Yaya Dacta ' Ko alamar motsi bata ji ba Ɗan sake ɗaga sautin tayi tana sake ƙiran sunan sa wannan karon har da "Auntie Sofi .Amma kamar basa gidan ' Wani irin tsinkewar zuciya ta ji da ya sa ta kusan faɗuwa saboda gurnanin kare da taji a daf da ita . A daskare ta waiga bata ga karen ba sai fa gurnanin da take cigaba da ji , addu'o'i ta fara yi da duk ayar da tazo bakin ta bata saki sai ta kai ƙarshen ayar . A hankali ta fara yin baya-baya har ta koma kan kujera, haushin da karen yayi da ɗan ƙarfi da yake bata tabbacin yana cikin falon yasa bata san lokacin da ta shige tsakankanin kujera kudundune ta cure guri ɗaya duk kuwa da rashin sararin wajen . Bata san tsawon lokacin da ta ɗauka a haka ba sai ji tayi hannu na ƙoƙarin zaƙulo ta a wajen da bata kai ga fahimtar hannun mutum ne ko kuwa na karen da zuwa yanzu ta fara tunanin aljani ne ba. Wani irin ihu ta sa tana runtse idanun ta gam cikin fitar hayyaci . Riƙo ta Doctor Hamza yake yi tana kufcewa ba tare da ta daina ihun da take yi ba , Jijjigata yayi da ƙarfi yace "Ke Amina ki nutsu ki dawo hayyacin ki me yake damun ki ne haka ? Tsoron ki yayi yawa . Jikin sa ta shige tana wani irin kuka cikin muryar kukan tace "Yaya Dakta dan Allah ka mayar da ni gida wallahi idan ba haka ba karen nan zai kashe ni .. "Wafaa ki nutsu babu kare a gidan nan ba mu da kare tsoron ki ne ya cika yawa ki daina saka tsoron abu haka a ran ki da har zai dunga yi mi ki gizo . "Akwai wallahi ba gizo bane akwai kare yanzu ma yana nan anan ina jin kukan sa . "Wai me ya faru ne wannan take yiwa mutane ihu da daren nan ? Kamar wata sabon kamu ... "Sofia ki yiwa mutane shiru please . Hamza yace haka a harzuƙe da jin haushin ta . Yana shafa kan Yakaka wacce take ta ajiyar zuciya a ƙirjin sa . Ƙyeɓe baki Sofia tayi kafin ta tausa murya tace "Doctor ni yanzu ka zo muje muyi wankan mu ka san dai kullum kaina kake hana ni zama da janaba. Kamar wacce wuta ta jaa ta Yakaka ta raba jikin ta daga na shi , kallon wasu 'yan daƙiƙoƙi ta yiwa ƙwarar idanun sa da suke cike taf da so da tausayin ta , ta sauƙe nata idon ƙasa tana jin wani irin abu mai nawi yana danne mata zuciya . Da sauri Doctor Hamza ya taka yana son sake riƙo ta , sai ta sake gocewa cikin muryar ta da kuka ya duƙusar tace "kar ka taɓa ni Yaya Dacta kaje kayi wanka . Bata tsaya ba sai ta juya da sauri dai-dai da sauƙar wata ƙwalla da bata san takaimai ta mece ce ba daga cikin idanun ta nufi 'yar hanyar da zata kai ta ɗakin sa tana jin tsoron da ya cika mata rai na raguwa sakamakon wani baƙon yanayi da zuciyar ta bata gama tantancewa da shi ba da yake mata ciwo a zuci fiye da tsoron. Wata 'yar ƙaramar dariya Sofia tayi da yasa Doctor Hamza da duk ya jikin shi yayi sanyi kamar wani mai laifi ya mayar da ganin sa kan ta tana tsaye daga ita sai ɗan wani guntun towel da iyakar sa cinya . Ƙaramin tsaki yayi yana hararar ta yace " Sofia ki dunga sanin abun da kike yi please . Za ta yi magana ya ɗaga mata hannu tare da kewaye ta ya wuce ɗakin sa . Da shigar sa ɗakin ya ɗora idanun sa akan ta tana kwance akan Sofa ta bada baya da alama tayi shirin bacci domin ta rufu da dogon hijabin ta daga wuya har ƙafar ta . Wani irin tausayin sa ne ya tsirga masa baki ɗaya ya rasa me yake damun ta take irin wannan tsoron shi dai tunda ya san ta ya san ta da tsoron kare amma bai san abun nata yayi ƙamari haka ba . Bai ce ƙala ba kamar yadda ita ma bata nuna alamun ta san da shigowar sa ɗakin ba ta ya wuce Banɗaki . Yakaka da idanun ta suke rufe tunda ya shigo ɗakin ta buɗe idanun ta a hankali tana jin yadda damuwa take ƙara mata yawa har ta rasa da wanne zata ji ? Da tsoron Sofi wacce ta mata barazanar da take da tabbacin zata iya aikata mata abunda ta ce ko kuwa da tsoron karen da yake gidan yake rayuwar sa da take da tabbacin Sofi ta san da zaman sa tunda tare ta fara ganin su . Gefe guda kuma ga ciwon da take ji kan yadda zuciyar ta ke ƙenƙesa mata rashin so da shi kan sa Doctor Hamza ya fara gwada mata banda haka ita ta wuni da yunwa ƙarƙashin horon Matar sa , shi kuma tunda ya dawo banda nan-nan da matar tasa da yake yi suna naniƙar juna baya ta tata da take baƙuwa a tsakanin su dan saboda tsabar cin zarafi ma daga zuwa ya ƙira ta shine.'... Ai ita ba yarinya ƙarama bace ta san abunda ya tsaya yi da matar sa , duk da tasan yana son Matar sa amma bata san son da yake yi mata ya kai ya mayar da ita wofi ba a dararen su na farko a rayuwar aure , tun yanzu ma kenan Sofi ta fara janye shi lokacin da yakamata ace da ita yake tare ina kuma a gaba ? Kalaman Sofia suka fara dawo mata da take gargaɗin ta kan haɗa shimfiɗa da mijinta "to a yadda ta ishe shi ɗin nan ma ita yaushe zai wani kula ta ? Ita dai ai kawai zata zauna ne ta ga yadda rayuwa zata mata amma bata tunanin wani farin-ciki irin wanda ake samu a rayuwar aure . Ko da ya fito tsayuwa yayi a kan ta bayan ya sanya riga da wondo na kwanciya bacci , a hankali cikin tausasa murya ya ƙira sunan ta "Wafaa , shiru tayi kamar bata ji shi ba . Jikin sa ya ba shi idanun ta biyu tana jin sa dan haka ya taka a hankali ya matsa tare da zama a bayan ta jikin sa na gugar nata . "Wafaa nasan kina jina ta shi muje na baki abincin nima yunwa nake ji . Shiru ta sake yi , ganin haka ya sa hannu ya juyo da ita bayan ya janye hijabin da ta rufu , idanun ta da suke ƙasa-ƙasa yake son kallo amma taƙi da kyar ta iya cewa "yaya dacta nifa naci abinci na ƙoshi . "Meyasa kika ci kika barni ? Daga yau idan ba bana gida ba kar ki sake cin abinci ke kaɗai ba tare da ni na baki ba kin ji ? Shiru tayi masa . Sake sassauta murya yayi saboda ya fara fahimtar kamar fushi take yi da shi abunda kuma ba halinta bane ita mace ce ma'abociyar fara'a da yawan murmushi. "To yanzu muje ki zuba min ni na ɗan ci ko kaɗan ne kin ga yunwa nake ji sosai . Ɗan jim tayi kafin tace "to . Tsayawa yayi yana kallon fuskar ta da ta ɗan kumbura kumatun sai ya ga kamar daɗa kyau tayi "Wafaa kome kika yi sai kiyi kyau da kike fushi kamar kar kiyi dariya idan kina murmushi kuma bana so ki daina saboda fara'ar ki haɗe take da farin-ciki na Ɗago kai tayi ta ɗan kalle shi tana jin tasirin kalaman sa har a cikin ran ta , a hankali tace "mu tafi ka ci abincin . Da suka koma falon ta zuba masa abincin dai-dai cikin sa yana ci yana ɗan kallon ta da tayi shiru tamkar mai tunani kafin ya fahimci gyangyaɗi take yi . Bata san lokacin da ya gama cin abincin har ya Sha shayin sa ba saboda kwantar da kai tayi a jikin kujera sosai take bacci . A hankali ta ji ya taɓa ta da yasa ta firgit ta buɗe idanun ta da suke cike da bacci ta kalle shi , "Mu je ki kwanta Wafaa dare yayi sosai . Kama hannun ta yayi suka shiga ɗaki bayan ya kashe wutacen falon da duk wasu na'ura . Sofia wacce duk abunda suke tana falon a laɓe daga lungun kitchen da yake da ɗan duhu ta saɗaɗo ta fito , Wani ƙaramin ɗaki da yake matsayin na 'yan aiki nan ta buɗe ta shiga bayan ta ɗau kwanon miyar da sauran miya da nama yake ciki , Tana buɗe ɗakin Sam da yake kwance ya taso da gudun sa yana ɗan gurnani , shafa kan sa tayi kafin ta ajiye masa kwanon a gaban sa . Wani irin ɓacin rai take ji bata ƙi ba ta ɓace ta ɓulla cikin ɗakin Doctor Hamza ta ga me suke yi shi da Yakaka ? Duk da dai tasan ba shi da buƙata amma ita fa ko kallon Yakaka bata so ya dunga yi "Ya zama dole nayi wani abu akai ba zan iya zuba ido haka ina kallon su ba kissa kaɗai ba zata gamsar da ni ba kar na tsaya galala shegiyar yarinyar nan ta min shigar basaja . Ta furta hakan a sarari lokacin da take barin ɗakin ta jaa ƙofar ta kulle tana nufar ɗakin ta . Duk yadda Yakaka ta so Doctor Hamza ya ƙyale ta ta kwanta kan kujera ƙi yayi dan dolen ta da kuma baccin da ya riga ya ci ƙarfin ta ta dawo kan katifar daga can ƙarshe ta kwanta . Tana kwanciya kuwa bacci ya ɗauke ta , fahimta da yayi baccin ya mata nawi ya sa shi jaan jiki a hankali ya matsa ya haɗa ta jikin sa , yana jin wani irin nutsuwa ta musamman tana bin jijiyoyin jikin sa yayi musu addu'a yana rufe ido bacci mai daɗin gaske ya ɗauke shi . Da asuba shi ya riga ta tashi , motsin da yayi da kuma fitsari da ya matse ta yasa ta buɗe ido a hankali . Cikin nutsuwa ta fara fahimtar a inda take kwance kan ƙirjin Doctor Hamza . Wani irin bugu nata ƙirjin yayi abu na farko da ya fara safkowa kwakwalwarta gargaɗin Sofi . Kamar an soke ta ta miƙe daga jikin sa ta fara ƙoƙarin matsawa ta sauƙa daga gadon . Idanun sa ya mayar ya rufe yana sake riƙo ta da ɗan tsauri ya jawo ta ta dawo kan sa "gudun me kike yi bayan kin kwana kin hantse kina bacci mai daɗin da baki taɓa yin irin sa ba . Ya furta hakan muryar sa a ƙasa sosai . Yakaka cikin yanayi na tsoro tace "Yaya Dacta dan Allah ka kyale ni kar Auntie Sofi ta shigo ta gan ni . Da sauri ya buɗe idanun sa jin abunda tace . "Sofi kuma ? Me zai kawo Sofi ɗakin nan war haka ? Shiru Yakaka tayi tana kwantar da kai , "kin cika shirme Wafaa ke Matata ce ko Sofi ta gan mu ba abunda zai faru . "Yaya Dacta kar a shiga Sallah . Ta tunasar da shi cike da son ya kyale ta . Yana rungume da ita ya miƙe zaune yana zaunar da ita a cinyar sa yace "zan tafi Masallaci na dawo kar kiji tsoron kome kin ji ko ? "To tace tana miƙewa daga kan shi . Shima miƙewa yayi ya shiga banɗaki yayi alwala ya fita masallaci . Yana fita ita ma ta shiga banɗakin dan ta kintsa jikin ta . Lokacin da ta fito kan ta yana ƙasa tana gyara jikin ta bata ankara akwai mutum a ɗakin ba sai da ta zo tsakiyar ɗakin ta ɗago kai . Idanun ta suka faɗa cikin na Sofi wacce take mata wani irin kallon da ya firgita ta. Assalam Alaikum Masu karatu tare da fatan alkhairi . Kuyi haƙuri da wannan bai kai yawan yadda aka saba ba , jimawar ne nima bata min daɗi shi yasa na baku wanda ya sauwaƙa . Idan dama ta samu zaku iya sake ganin cigaba nan da kwanaki uku insha Allah . Nagode . [3/19, 5:14 PM] +234 706 503 6187: Mafari. . ( Hargitsin Rayuwa ) Umm'muaz 53 Tsayuwar minti ɗaya zuwa biyu tayi tana kallon ta kafin ta ƙaraso gaban gadon ta zauna ba tare da tace mata ƙala ba . Hakan da tayi ya sake ƙular da Sofia dan haka a fusace tace " zaɓi na zo baki ko dai yini tare da Sam ko kuwa ki fice daga gidan nan ki tafi can inda kika saba zuwa yawon ki a garin nan idan shi da ya ajiye ki ya dawo kin dawo dan yinin ki da ni a gidannan bana jin zan iya jurewa . Yakaka wacce kan ta ke ƙasa har Sofia ta gama bayanin ta bata ce mata kome ba tamkar dai bata jin yaren da Sofia take yi ta miƙa hannu a hankali ta ɗau wayar ta ta fara dannawa ba tare da tasan me take yi ba ' Hakan da tayi ba ƙaramin tunzura Sofi tayi ba a fusace tace "Dan Ubanki watau ga mahaukaciya tana magana kin wani yi banza dan....' Kamar an safure ta Yakaka ta miƙe daf da Sofi ta zo ta tsaya idanun ta ƙyar akan ta cikin muryar ta da bata cika ƙarfi ba tace "Duk wani cin mutumci da zage-zagen ki ya tsaya a iyakar kaina , kar domin kin ga ina yin shiru kiyi zaton za ki iya zagin iyayena na ƙyale ki . " ban ajiye iyayena kurkusa ba idan ke kin raina naki iyayen na..... Turo ƙofar da aka yi yasa su duk biyun waigawa . Doctor Hamza turus yayi yana kallon su kafin ya ƙaraso fuskar sa cike da mamaki ya tattara ganin sa kan Sofi wacce har kawo lokacin bata farfaɗo ba daga ruɗanin da ta shiga kan ji da tayi Yakaka ta mayar mata da Martani har ma tana ƙoƙarin rama zagin da ta mata. "Sofia me ya faru ? Me kika zo ... Sai yaƙi ƙarasawa ya ɗan riƙo hannun ta ganin wani irin huci da take yi ,so yake ya jaa ta waje . Amma sai ta ƙi da ƙarfi ta warce hannun ta kafin ta fashe da wani irin kukan baƙin-ciki . "Na shiga ukuna Yakaka ni kike zagi ? Iyayena kike zagi Ni-ni kika zaga ? Yakaka uwata da ubana kike zagi ? Daga kawai na shigo na tayar da ku Sallah ? Yakaka wacce ta cika da mamaki da tsoro ta ɗago kan ta fuskar ta ɗauke da mamakin makircin Sofi da bata saba da irin sa ba tayi rau-rau da ido tana kallon Doctor Hamza wanda shi ma ita yake kallon fuskar sa a ɗaure , ta juya ga Sofia tace "ki ji tsoron Allah ni na zage ki ? Ba ke kika zage ni ba ? Ina ke ce kika shigo kawai kika fara zagi na har da Babana ? Sofia ta zaburo zata yi magana Doctor Hamza ya dakatar da ita da cewa "saurara Sofia wai me yake damun ki ne ? Ya za ki shigowa mutane ɗaki haka da sassafe ? Zata yi magana ya sake katse ta wannan karon muryar sa a kaurare yace "Sofia bana son tashin hankali da fitina , ran ki zai yi mummunan ɓaci muddin kika ce ... Sofia wacce take jin zuciyar ta kamar zata fashe ganin Doctor Hamza yana shirin birkice mata kuma a gaban Yakaka . Nan take ta haɗiye kukan kissar ta ta murje ido cikin salon ta na goggagun matan da suka raina mazajen su kunya kuma ta mata nawin ɗauka ta gatsina fuska da buɗaɗɗiyar murya tace "Wannan wane irin rashin adalci ne kake fara rabawa a tsakanin mu tun yanzu ? Kenan dan tana ɗakin bani da ikon shigowa ɗakin ka a duk lokacin da na so ? "Sofia ki wuce ki koma ɗakin ki kar ki ɓata min rai ki ɓata min lokaci . Buɗe baki tayi kamar zata ce wani abu sai kuma ta fasa tana mayar da ganin ta kan Yakaka wacce ita ma ita take kallo , da haƙoran ta ta cije leɓen ta na ƙasa tana yiwa Yakaka wani irin mugun kallo tayi ƙwafa kafin ta juya a fusace ta fita a ɗakin tana wani irin bugo ƙofar da har sai da Yakaka ta firgita . Tsoron Sofi da ya ɗan yi ƙaura saboda zuciya da tayi da ta zagi Baban ta taji yana dawowa sabo fil ,ta tuno da zaɓin da tace ta bata kan ta zauna ta yini da kare a ɗaki irin na jiya ko kuma ta fita ta bar gidan to ta tafi ina ?? Yaya dacta ma ai ba zai bari ta fita ko da ƙofar gida bane kuma a can ma an mata nasiha kan fita ba mutumcin matar aure bane a dunga ganin ta a titi haka siƙau muddin ba lamarin zumunci mai ƙarfi ko aiki ko kasuwanci zata fita yi ba . Hannun sa da ta ji a ƙugun ta shi yasa ta sauƙe ajiyar zuciya , tana jin lokacin da ya sako fuskar sa ta gefen wuyan ta ƙamshin turaren sa na game mata hanci , muryar sa kamar ba shi ya gama kurara Sofi yanzu ba yace "tunanin me kike yi Wafaa ? Bana son kina yawan tunani na faɗa miki . A hankali ta juyo ba tare da ta fita a tsakanin hannuwan sa da ya kewaye ta da su ba tana yin ƙasa da murya tace "Yaya Dacta wallahi ban zage ta ba ku.... "Shitt yace yana ɗaura hannun sa akan laɓɓan ta da yasa ta ɗago kan ta tana kallon ƙwarar idanun sa da suke cike da tausayin ta "Ba sai kin min bayani ba Wafaa na san halin Sofia , kiyi haƙuri zan ɗauki mataki ba zan bari ta ci zarafin ki ba da ke da ita duk matan Aure na ne kiyi haƙuri kin ji ko ? Wata sassanyar ajiyar zuciya tayi jin daɗin bai yarda da sharrin da ta so ƙulla mata ba " Nagode Yaya Dacta . Murmushi ya yi mata kafin ya sake matso da ita jikin sa kamar mai raɗa yace "mu je mu kwanta kafin lokacin tafiya ta aiki . Da sauri ta girgiza kai kafin tace "Yaya Dacta kitchen zan tafi na yi girkin abin karyawa kafin ka tashi bacci. Zama yayi a bakin gado yana zaunar da ita a cinyar sa yace "No Amarya ce ke Wafaa bai ma kamata kina shiga kitchen ba har sai mun gama amarcin mu ko ? Ya ƙarasa da sigar tsokana yana ɗaga mata gira . Ɗan murmushi tayi tana miƙewa tsaye "zan tafi kitchen Yaya Dacta bana so ka tafi office baka yi breakfast ba . Da gama faɗin haka ta taka tana barin ɗakin , fuskar sa ɗauke tattausan murmushi ya bi ta da kallo salon kulawar da ta gwada masa ya burge shi daban da na Sofi wacce bata iya kula da duk wasu lamuran nasa ba sai fa gwada haukar So a sarari . Bai kwanta ba sai ya jawo littatanfan sa na addini ya shiga karatu. A kitchen cike da azama irin na matan da suka gogu da aiki Yakaka ta ɗora ruwa kafin ya tafasa ta kwaɓa fulawa da baking powder sai 'yar zuma da ta sa a madadin sugar . Lokacin da ruwan ya tafasa ta wanke shinkafa fara ƙal ta tuwo ta zuba tare da Sugar sannan ta zuba spices da ake amfani da su wajen haɗa shayi . Kafin shinkafar ta nuna , ta ɗora mai ta fara soya pancake da har ya fara tashi saboda ɗumin wajen ' kafin ta gama shinkafar ta tayi ligib dan haka ta dama madarar gari mai yawa ta juye akan shinkafar ta da tayi ligib tana juyawa yayi kauri kamar talge shinkafar kuwa tabi cikin madarar, ɗan manshanu kaɗan ta zuba aiki ta kashe Sugar ta bari. Da ta gama soya pancake bata bar kitchen ɗin ba sai da wanke kwanukan ta goge ko'ina tsaf . Sannan ta buɗe fridge ta ɗauko Strawberry ta wanke shi tsaf ta yanka shi a tsai-tsaye bowl ta ɗauko mai kyau tazuba basisen da yayi nar-nar da shi ya kwanta fari ƙal , sai ƙamshin man shanu da kayan ƙamshi yake yana ɗaukar Ido . Bayan ta zuba iya adadin yadda ta ke ganin yayi sai ta jera Strawberry ɗin a kai , ta rufe , ta ɗau wani bowl daban kuma ta zuba pancake . Bata juya ba amma jikin ta ya bata da tsayuwar mutum a bayan ta dan haka ta juya da sauri , Ajiyar zuciya tayi ganin Doctor Hamza ne shirye yake tsaf cikin shirin sa na zuwa wajen aiki a hankali ya tako har inda take yana bin fuskar ta da kallo da ita ma shi take ta kallo cike da burge ta da yayi kamar wani bature ya tsuke cikin lounge suit launin shuɗi Mai duhu . Yana mata murmushi ya shafa kumatun ta , "Wafaa wannan kallon fa ? Yace da sautin da yake tsakanin maƙoron sa . Sunkuyar da kai tayi a dan kunyace da 'yar ƙaramar murya tace "ba kome har ka shirya ? Nima na gama girkin . "Naso na makara ma wafaa , me kika girka mana ? Ya furta hakan yana zarcewa da hannun sa ya buɗe abincin da ta haɗa , da kallo ta bi fuskar sa cike da son ganin yanayin da zai nuna . Buɗe baki yayi cike da jin daɗi sai kuma yayi murmushi "Basisee ? Wow Wafaa ashe kin iya girki ? Kamar kin san na daɗe rabo na da na ci Basisee . Murmushin jin daɗi tayi tana ɗaukar farantin da abincin ke kai tace "Yaya Dacta to muje ka ci tunda ka ga har ka makara . Bayan ya zauna a kujera ta Zuba masa basise a Plate ta ɗeba masa pancake ɗin ta zuba a gefe. Duk abunda take yana bin ta da kallo cike da so da sha'awa komen ta a tsaftace dai-dai da yadda yake so . Bayan ta zuba masa yayi bismillah ya ɗau pankcake ya dangwali Basisen ya kai bakin sa ya gutsura Daɗi da ƙamshin girkin ya ratsa shi , a karo na biyu Yakaka bata tsammata ba ta ga ya nufo bakin ta da Pancake , Noƙewa tayi tana kallon shi tace "idan ka gama nima zan ci , "Buɗe bakin ki Wafaa, yace muryar sa da sanyi amma ƙwarar idanun sa na mata umarni . A hankali ta buɗe baki ya saka mata yana bin ɗan ƙaramin bakin ta da kallo yadda take cin abincin a kunyace ya so ba shi dariya "yarinya za ma ki sauƙe wannan kunyar ta ki ne a hankali " sannu kan hankali ya ciyar da su iya cin su da su duk biyun sun yi mamaki domin kusan duk suka cinye sai fa kaɗan suka bari da bai wuce cin ɗan yaro ba . Sauƙowar Sofia ya ɗau hankalin Yakaka da ta hango ta sai ta ji wani abu ya ɗan taɓa ran ta da bata san mene ne ba , ta sai ji kamar ta muzanta ganin irin kwalliyar da Sofia tayi cikin wani yadi da aka yiwa kyakkyawan ɗinkin Riga da Siket da suka kama ta ɗam. Tayi ɗaurin ɗankwalin zamani ƙamshi turaren ta ya riga ta isowa . A hankali Yakaka ta saci kallon Doctor Hamza ta ga yadda yake bin Sofia da kallo da alamun kwalliyar ta ta ɗau hankalin sa , ganin ta ta mayar kan ta , ta ga tun atamfar jiya da daren nan ce a jikin ta sannan ba wata kwalliya a tare da ita , duk sai ta fara ganin laifin kan ta "Amnee cewa tayi kullum ki dunga ƙwalliyar Safe daban ta rana daban ta dare daban ta kwanciyar bacci daban . Zuciyar ta ta tunasar da ita . Hakan yasa tayi saurin miƙewa kunnen ta na toshewa daga jin zantukan Doctor Hamza da Sofia da suka fara sabuwar gaisuwa ba'a ce sune ɗazu suke hayaniya ba . Sofia ta shafe fushin ta kamar kome bai faru ba . Taku biyu tayi ta ji hannu Doctor Hamza cikin nata ɗayan hannun sa kuwa riƙe da briefcase . "Wafaa ni zan tafi ba za ki min rakiya ba ? Murmushin yaƙe tayi tana ɗan kallon Sofia tace "zan tafi nayi wanka ne . Wata 'yar dariya Sofia tayi kafin tace "anya kya yi wanka yanzu ? Ko da ... Da sauri Doctor Hamza ya katse ta lokacin da yake sakin hannun Yakaka yace "Sofia na jima ban ji daddaɗan girki irin wannan ba ba domin Amnee kar ta hukunta ni ba zan ce ma ban taɓa cin basise mai daɗin wannan ba Sofi ki koyi girki ke ma zan ji iri.. Taɓe baki Sofia tayi tana hararar bayan Yakaka wacce ta riga ta juya tana barin wajen zuwa ɗaki kafin ta dawo da ganin ta kan Doctor Hamza . Fuskar sa a ɗaure yace "na faɗa miki ki daina neman fitina hakan ba kome zai jawo miki ba illa raini yarinyar nan dai a haife ma kin kusa haihuwar ta. Kamar an soke ta da tsinin mashi haka Sofia ta ji , "ita zai ce ta haifi Yakaka ? ƙanƙance ido tayi zata fara jaraba yayi wucewar sa cikin ɗaga taku yana barin falon ran sa cike taf da jin haushin korar masa Wafaa da tayi bata bari sun yi sallama ta masa rakiya ba . Ta jima a tsaye a wajen tana rarrashin zuciyar ta da take ingizata akan ta je ta yiwa Yakaka dukan tsiya idan ya dawo ya ga banbancin shekarun a zahirance ' Sai dai ɗaya ɓarin zuciyar ta da yake cike da tsoron abun da hakan zai jawo ya hana ta aikatawa. Sai da ta furzar da wata iska mai zafi sannan ta juya ta nufi ɗakin da take ɗaure Sam . Yana kwance magashiyan kamar gawa , ƙafar ta tasa ta haure shi amma bai motsa ba " Dan ubanka kai ma ka tashi haka kaje kayi aikin da na kawo ka domin yi , ni inaga wannan maganin ma kamar ya maka ƙarfi yau ba zan baka shi ba . Yakaka wacce har ta shiga wanka ta tuno da abincin ta na rana da ta ɓoye a kitchen cikin dabarar da take son yi , dan haka ta ɗaura towel ta zura hijabin ta ta murɗa ƙofar ta fito sai da tayi dube-dube ta samu tabbacin Sofia bata nan sannan da sassarfa ta tafi kitchen ta ɗauko sauran Basise da pancake da ta juye a warmer ta rufe ta nufo ɗaki. zuwan ta tsakiyar falon yazo dai-dai da fitowar Sofia jaye da karen ta da yake ta turjewa yana wani ɗan kuka . Kallon-kallo suka yi a tsorace Yakaka ta jaa baya tana neman hanyar gudu cikin daƙiƙu kaɗan Sofia ta fahimci abunda Yakaka take shirin yi . Dan haka ta zaburo bayan ta saki karen, da ganin haka Yakaka ta zuba a guje ta faɗa ɗaki da bata nesa da shi sosai tana shiga ta dire warmer ta danna ƙofar ta murza key bayan ta kulle ta zare shi daga jikin ƙofar dai-dai da ƙarasowar Sofia . Wani irin duka Sofia ta kaiwa ƙofar kamar wacce ta sha giya ta shiga ƙundume-ƙundumen zagi tana cewa sai ta ga bayan Yakaka . Yakaka wacce take jingine da jikin ƙofar daga ƙasa da ta zame ta zauna ji tayi hawaye na sauƙa a idanun ta wacce irin masifa ce wannan ? "Ai kin kulle ƙofa a banza ki jira zan nuna miki iyakar ki zan nuna miki cewa nan gidana ne da baki isa min shamaƙi da wani ɓangare a cikin sa ba. Tana jin lokacin da ta juya ta bar wajen bayan ta gama faɗin haka , ajiyar zuciya tayi ta miƙe tana ɗauke warmer ɗin daga wajen ta ajiye a gefen gado , Duk da ran ta na mata ciwo da irin yadda take rayuwar rashin ƴanci amma ta ji daɗi da yau Sofia ba zata samu nasarar turo mata kare kamar yadda ta ɗau alwashi ba ita daman ko babu kare a gidan ma yinin falo ba nata bane muddin Sofi na shawagi a gidan . Wanka ta shiga ta ƙarasa ta kusa fitowa ta ji kamar an buɗe ƙofar an shigo ta ɗan kasa kunne bata ji motsi ba sai dai ƙarar rufe ƙofar da ta sake ji yasa a tsorace ta ɗauraye jikin ta ta fito . Abun da ta gani yasa numfashin ta yin gargada 'Sam ne Sofia ta sake kawo mata shi kenan tana da makullin ɗakin ? Yau ma so take tayi yini makamancin na jiya ? Wani irin daskarewa take ji zuciyar ta na yi tsanar Sofi na ratsa kowanne lungu da saƙo na ran ta "sofia wace irin Azzaluma ce haka ? Da gaske idan bata bar gidan ba watarana Sofi zata kashe ta . Kallon karen take yi tana jin yadda bugun zuciyar ta ke sauyawa tamkar jinin jikinta ya tsinke . Laɓɓan ta na karkarwa ta fara jaan ayoyi tana yin baya-baya ta koma cikin banɗakin ta rufo ƙofar , sai kawai ta fashe da kuka ,ita tun da ta san kan ta a matsayin mutum babu wani abun da take jin tsoro sama da kare , Bata son kare ta yadda ko da takun ƙafar sa ta gani a cikin ƙasa sai ta ji bugun zuciyar ta ya sauya Allah ya ratayawa ruhin ta tsoron kare . Ta jima a zaune cikin banɗakin tana tunanin mafita "shin haka zata zauna kullum Sofi na azabtar da ita ta hanyar turo mata kare ? Ba zata iya ba domin watarana zuciyar ta zata gaza jurewa tsoron da take shiga sanadin haka sai ta mutu . "To kuma idan ta faɗa me zai biyo baya watakila Sofi ta kashe ta da wuƙa da kuma ta san ba wanda zai san ita ta kashe ta domin daga jiya zuwa yau ta hango wani lamari tattare da Sofi da ya zarce mugunta sai dai a ƙira shi rashin imani. " Wai kuma da gaske Yaya Dacta bai san da kare ba a gidan ? Anya gaskiya ne ? Tunanin ta ya katse lokacin da ta ji karen na wani irin kuka ciki-ciki kamar gurnani , can kuma ta ji yayi shiru sai ta ɗan matsa kaɗan ta leƙa ta ƙafar makulli inda ta bar shi a kwance a can ta hango shi ya yada kai gefe . Ta koma ta zauna tana tunanin yau kuma baya tsalle-tsallen ? Har azahar tana cikin banɗaki har gyangyaɗi tayi ta farka lokacin ma ana ta sallah , ta sake leƙawa ga mamakin ta har yanzu fa Sam a inda yake anan yake kwance . Shiru tayi tana nazarin sa da ta ƙura ido sosai sai ta ga kamar ma bacci yake . yunwar da take ƙwaƙwular ta ita ta tunasar da ita cewa fa lokacin cin abincin ta na rana yana ƙoƙarin wucewa . Tunanin da ya ɗarsu mata a rai a dai-dai lokacin ya sa tayi wani ɗan zullo tana dafe ƙirji a fili tace "wallahi bazan iya fita ba watakila idon sa biyu . Can bayan kamar mintoci talatin da ta gama nazarin Sam ta haƙaƙe bacci yake yi sai ta buɗe ƙofar a hankali ta fito saɗaf-saɗaf ta nufi inda ta ajiye abincin ta kafin ta ɗauka sai da ta buɗe ƙaramin fridge da yake ɗakin ta ɗau ruwan roba mai sanyi guda ɗaya . Tana juyawa kamar ance masa ya miƙe kawai sai ganin sa tayi akan ƙafafun sa huɗu yana kallon ta . Wani irin ihu ta sa tana sakin ruwan hannun ta da warmer ɗin ta tarwatse a ƙasa da hakan yasa Sam ya dako tsalle yana zuwa a yunwace yasa bakin sa akan Basisen ya fara lasa yana haɗawa da pancake yana cinyewa bai ko bi ta kan Yakaka ba wacce tayi suman tsaye tana jira ta ji shi a kan ta yana kachal-chala mata tsoƙar jiki da faratan sa . Wani irin riƙe jikin ta tayi har yatsun ta na shiga cikin carfet ɗin da yake shimfiɗe a ƙasa ji da tayi yana lasar rumfar ƙafar ta da basisen ya zuba akai a lokaci ɗaya wani irin tsoro mai haɗe da raɗaɗi ya ratsa tun daga ƙafar ta har ƙwaƙwalwar ta ta saki wani irin ihu da ya ratsa baki ɗayan gidan . Numfashin ta kuma ya shiga ƙoƙarin barin jikin ta . Ba zata iya sanin iyakar daɗewar da tayi ba kawai dai ta ji wani irin sanyi yana ratsa rumfar ƙafar ta da yasa ta buɗe ido a hankali . Abunda ta gani ya matuƙar bata mamaki lokaci ɗaya da shiga sabon ruɗani . Sam ne ta yake ta faman jido robar ruwan sanyi daga cikin fridge a bakin sa yana zuwa yana ɗora mata a jiki tamkar wanda aka sa shi yana yi yana kaɗa jela. Tsam tayi tana kallon sa da idanun ta da suka rine jazur , sai da ya jido ruwan cikin fridge ɗin kaf sannan ya dawo gaban ta ya tsugunna yana kallon ta tamkar mai jiran ta masa wani umarnin Sai zaro harshe yake yana lallago . Kallon sa Yakaka tayi ta kawar da idanun ta zuwa lokacin har ta kai maƙura a tsoro alhalin babu mai ceton ta ba kuma wajen tsira dan haka ta fara dawowa cikin hankalin ta . Tun tana tunanin zai bazamo kan ta har dai ta fahimci baya wani yunkuri na cutar da ita da ya wuce banga-banga da yayi a gaban ta dan haka a hankali ta kai hannu ta ɗau ɗaya daga cikin ruwan da ya jera mata bayan ta gama jujjuya robar ruwan a hannu ta ta ɓalle murfin ta sha ruwan da ɗan yawa kafin ta sauƙe gorar . Mamakin ta ya ƙaru lokacin da ya sake kai fuskar sa ya daɗa turo mata wata gorar ruwan kusa da ƙafar ta . Tana kallon sa ta kai hannu ta ɗauka , sai ta ga yayi baya ya kwanta shirim! daga nesa kaɗan da ita . Wata ɓoyayyar ajiyar zuciya tayi tana jin 'yar guntuwar nutsuwa na shigar ta sai ta gyara zaman ta da bata san yaushe ma ta zaunan ba ta miƙe kafafun ta da suka mata tsami saboda daɗewa da tayi a durkushe . Cikin siririyar muryar ta ta fara yin karatun Alqur'ani bayan ta jingina kan ta da jikin gado. Wata irin nutsuwa ce mai girma ta mamaye ta da ta lura hatta Sam shi ma ya samu kwatankwacin nutsuwar domin kwance yayi shiru ya kwantar da kunnuwan sa lanbar lokaci-lokaci yana kaɗa jelar sa . Lokacin da ta fahimci rana ta kusa faɗuwa a hankali ta miƙe abun da ya bata tsoro a lokacin bai wuce ganin yadda shi ma Sam ya miƙe ba tsam ya tsaya ' da sassarfa ta nufi banɗaki tana waigen sa ganin yadda yake bin ta , yasa ta ɗan ƙara da gudu ta shige banɗaki bayan ta shiga ta rufo ƙofar kafin ta fara wanka sai da ta leƙa shi ta ga ya tsugunna a bakin ƙofar . Cikin nutsuwa tayi wankan ta , kan ta tsaye ta murɗo ƙofar ta fito , yana ganin ta ya matsa mata a hanya ta wuce kafin ya bi bayan ta zuwa gaban madubi. Ɗan kallo shi tayi tana mamakin sa cikin ran ta ta aiyana "ashe ma ba zai min kome ba ? Lokacin da ta gama shiryawa tsaf sai ta ɗauko sabbin kayan ta wani lallausan yadi da aka yiwa adon manyan furanni launin ruwan dorawa da fari , ɗinkin rigar iyakar guiwa irin ta matan N'djamena da aka mata tattara da roba daga kugun ta da ɗan guntun hannu . Ta ƙasa ɗan dogon wondo ne mahadin rigar da bai ƙarasa idon sawun ta ba , a fuskar ta bata wani cika kwalliya ba powder kawai ta shafa sai ta zizara kwalli a ƙasan idanun ta ɗaurin ɗankwalin da tayi sassauƙa ne ta nannaɗe gashin ta da shi ta baya yayi ɗan tum-tum ta ɗau turaren ta na humra ta shafa sai kuma ta fesa wani kaɗan da ta gani a gaban madubin ɗakin. Cikin nutsuwa duk kuwa da bibikon da Sam yake mata amma ta dake zuciyar ta tayi ƙam-ƙam ta hana tsoron da take ji har yana mata wani yam-yam a cikin jini ya yi tasirin da zai haukata ta ,ta fara tattara ɗakin duk inda Sam ya ɓata ta tattare ta goge da Moper ta gyara ko'ina tsaf har gado , tana yi tana kallon Sam da yake mayar da ta shi ƙafar a duk inda ta cire ta ta . Bayan ta gama gefen gado ta samu ta zauna ta ɗau wayar ta da bata san lokacin da aka wargaza mata ita ba batirin daban wayar daban a take sofi ta faɗo mata a rai tana zaton ita ta mata haka da wayar . Girgiza kai kawai tayi ta fara neman layin Hajja sai dai tayi ta ƙara daga can ba'a ɗaga ba. Ɗan saurarawa tayi lokacin da ta ji ana ƙoƙarin buɗo ƙofar ta mayar da hankalin ta ga ƙofar , Kamar wacce aka tunkuɗo ta Sofia ta buɗe ƙofar ta shigo , turus ! Ta jaa ta tsaya tana rarraba ido a ɗakin da yake tashin ƙamshin humrar Yakaka ba kamar yadda take zato ba ko'ina tsaf yana ɗaukar ido kafin ta tsayar da ganin ta kan Yakaka wacce tun shigowar ta kallo ɗaya kawai tayi mata ta mayar da ganin ta kan Waya duk kuwa da cewar ta tsorata amma taƙi yarda tsoron ya fito fili . "Sam . Sofia ta ƙira shi a tsawace da wata irin muryar da ba Yakaka kaɗai ba har Sam da yake kwance daga ƙasa kusa da ƙafafun Yakaka sai da ya tsorata ya miƙe a safure ya shiga haushi ba ƙaƙƙautawa. Sofia wacce a dai-dai lokacin duk wata dabarar ta tayi ƙaurar wucin gadi sai ta taho kawai fangam-fangam bayan ta zare takalmin da yake ƙafar ta ta takarkare iyakar ƙarfin ta ta kwaɗawa Sam tsinin takalmin a kan sa har sai da ya durƙushe. ,"Ɗan iska cewa nayi ka zo kuyi soyayya da ita ? ba cewa nayi ka cije ta ka kashe min ita ba? Wani irin kuwwa yayi da yasa Yakaka daka tsalle ta hau kan gadon tsoron ta yana dawowa sabo fil . Sofi bata ankara ba ta ji ya kawo mata wafta da sai da ta kusa tuntsurawa tana ɗaga Ido ta hango takalmin ta a bakin sa ganin yadda yake gurnani yana nufo ta yasa ta fara jaa baya mamakance , laɓɓan ta na ɗan rawa ta fara ƙiran sunan sa "Sam.Sam.Don't.... Ganin yadda yayi kan ta gadan-gadan ya san kasa ƙarasa kalmomin da take nufin furtawa sai juya ta ruga a guje Sam ya rufa mata baya da gudu da haushin sa da ya karaɗe gidan . Yakaka wacce jikinta har rawa yake tsabar tsoro da gudu ta duro daga gadon ƙafafun ta babu takalmi ta fito daga ɗakin kai tsaye hanyar fita a gidan tayi a ruɗe "har a ran ta ta zaɓi barin gidan akan ta zauna Sam ya gama da Sofia da take uwarɗakin sa ya dawo kan ta . Bata san da tahowar sa ba kamar yadda shima bai yi zaton fitowar ta ba a wannan lokacin suka ci karo. Gaba ɗaya ta faɗa masa a jiki ta chakume shi.. "Yaya Dakta wallahi kare nan zai cinye Anty Sofi ga su can ya bita da gudu zai kashe ta ya dawo kaina.... Da sauri ya ɗago ta tana sake ƙwaƙwume shi yanayin sa da galabaita sosai da tarin damuwa ya ɗago ta da kyar daga jikin sa bayan ya saki jakar hannun sa ta faɗi ƙasa ya riƙe fuskar ta a tsakanin tafukan sa . "Me yake damun ki ne Wafaa ? Waye yake tsorata ki da kare ? Faɗa min aina kike ganin kare ? Yaushe haka ya fara faruwa da ke ? Ya furta hakan idanun sa na tara ƙwalla saboda can daga cikin kan sa ya fara hasashen wani abu da baya fatan tabbatuwar sa a gare ta. Laɓɓan ta na rawa tace "wallahi akwai kare a gidan nan kullum da shi nake wuni a ɗaki , Sofi ,Sofi ita take kai min shi kum.... "Safiya ? Ya tambaya da wani irin yanayi a muryar sa bayan yanayin fuskar sa ya jirkitu da tsantsar ɓacin rai . "Eh , Ah' ah ba ita ba amma akwai kare yanzu ma ya bi ta zai cinye ta dan Allah dan Allah yaya dakta ka mayar da ni gida , zan koma Maiduguri ko kum.. "Shit yace yana rufe mata baki "wafaa ki nutsu ni duk bana fahimtar inda maganganun ki ke dosa kika ce Sofia take kai miki kare ɗaki ? Sofia ce take kawo kare gidan nan ? A hankali ta sunkuyar da kan ta tana jin zuciyar ta na rabuwa biyu sashi ɗaya tsoron Sofia yayi rinjaye ɗayan kuwa tsoron karen tare da son a fitar mata da shi daga rayuwar ta yana tunzura ta kan ta faɗi abunda ke faruwa. "Sofia ta ke tura miki kare a ɗaki ? Ya sake tambayar ta da taushin muryar da ta ratsa duk wani firgicin da ya cika mata zuci ya mata lulluɓi da nutsuwar da yasa ta dawo hayyacin ta dan haka ta ɗago kan ta a hankali ta motsa laɓɓan ta "Yaya Dacta aun.... "Amarya da ango kenan watau shigar sauri kika min Yakaka shi ne har kika riga ni fitowa taren Miji ? To ai shikenan na ci girma na bar miki . Sofia wacce take ƙarasowa ta furta hakan tana bin Yakaka da wani kallon da yasa Dactor Hamza kafe ta da ido yana nazarin ƙwarar idanun ta kafin ya bi jikin ta da kallo . "Sofia me ya same ki haka ? Ya rigar ki a yage ? Ya furta hakan yana mata nuni da jikin ta ba tare da ya saki hannun Yakaka ba . "Ƙusa ce ta yaga min . Ta furta hakan da yanayi na ko'in kula "Ƙusa ya tambaya muryar sa cike da shakku . "Eh Ta amsa masa a daƙile kafin ta matsa kusa da Yakaka ta zira hannun ta a cikin nata tana karyar da murya tace "muje na taya ki girkin kin ga tun ɗazu nake ta cewa ki tashi muje ki fara ina taya ki kika ƙi kika jibge a gaban Tv kina kallo . Yakaka wacce take kallon Sofia a tsorace ɗimbin mamaki na tasowa yana rufe ta ta ɗan kifta ido . "Sofia muje ciki . Doctor Hamza ya furta haka yana wucewa jaye da hannun Yakaka da ta bi shi da sauri bayan ta zare hannun ta daga cikin na Sofia da take jin sa kamar garwashi . A falon ya zauna kan ɗaya daga cikin kujerun Yakaka kuma ta zauna a ƙasa. Sofia da ta shigo daga bayan su ta zauna a kujerar da take kusa da wacce yake zaune bisa. Sai da ya ɗan nisa sannan ya tattara ganin sa akan Sofia fuskar sa ba alamar wasa yace "Sofia akwai kare a gidan nan ne ? Mui-mui tayi da baki kafin ta dafe ƙirji tace "kare dai Doctor ? Ta ina ya shigo mana ? Ko d... "Tambayar ki nayi kina sake tambaya ta Sofia ki bani amsa kawai . Hararar sa tayi ta ƙasan ido kafin ta taɓe baki "babu kare a gidan nan idan akwai kuma ni bana ganin sa . Yakaka wacce kan ta ke ƙasa ta ɗago da kan ta ta dubi Sofi da bata yi ƙasa a guiwa ba ta jefa mata wani kallon da yake ɗauke da saƙon gargaɗi . "Ok Yace yana miƙewa kai tsaye Sama ya dosa inda ɗakin Sofia yake da sauri ta miƙe ta bi shi a baya muryar ta tana ɗan shaƙewa tace "Doctor ko na zo ne akwai magana ? Ko wani abun kake nema ? Bai kula ta ba ya cigaba da tafiyar sa zuciyar sa tana sake ba shi tabbacin rashin gaskiyar Sofi da duk yadda aka yi tana da hannu wajen tsorata Yakaka , a ɗan tsukin ya fara gano wasu ɗabi'un Sofia da a da bai san tana da su ba . Sai dai duk inda yake zaton zai iya dubawa ya ga wani abu makamanci da kare da ake tsorata Yakaka da shi a gidan ya duba bai ga kome ba hatta cikin banɗaki da kitchen sai da ya duba . A gajiye ya dawo falon inda ya bar Yakaka a nan ya dawo ya same ta ya zauna akan kujera lokaci ɗaya ya dafe kan sa da ke ɗan masa ciwo bayan tarin gajiyar da take kassara masa gabɓan jiki . Shiru yayi har lokacin da Sofia ta ƙaraso wajen ta zauna fuskar ta wasai kamar an mata bishara . "Wafaa ya ƙira Yakaka da tsauri a muryar sa . A hankali ta ɗago kan ta. "Babu kare a gidan nan . Hawayen da bata san yaushe suka taru ba su ne suka silalo mata . "A karo na ƙarshe ina faɗa miki ba kare a gidan nan ya kamata ki kwantar da hankalin ki ki daina wannan firgice-firgicen da kike yi ko kina son ƙwaƙwalwar ki ta samu matsala ne ? "Docto wai daman akan haukar ..... "Sofia idan ina magana ki daina saka min baki please behave yourself. Yace yana mata wani mummunan kallo gaba ɗaya daga ƙasan ran sa yana zargin Sofia da bai san dalilin hakan ba shi dai zuciyar sa bata aminta da ita ba akan wannan matsalar da tayi sammakon shigowa rayuwar auren sa da Yakaka da ko kaɗan abun bai masa daɗi ganin ta koyaushe a firgice tana guje-guje da safure-safure yana ƙona masa rai tare da sauƙar masa da gajiya . "Wafaa ya ƙira ta a tausashe , ta ɗago kan ta da idanun ta da suke narke take kallon sa . "Zan yi shirin Masallaci idan na dawo daga Sallah zamu je mu ci abincin kar ki shiga kitchen yanzu dare yayi . Langaɓe kan ta tayi kawai bata amsa ba ko kaɗan bata son ya matsa ya bar wani sarari tsakanin ta da Sofi . Mayar da kallon sa kan sofia yayi wacce take ta faman hura hanci tana kokawa da zuciyar ta da take jin har wani toroƙo take kamar za ta fashe "Sofi anjima ina so nayi magana da ku baki ɗaya . Bai jira amsar ta ba ya miƙe , Yakaka ma cikam! Ta miƙe tana riga shi wucewa ta yi hanyar ɗakin su . Da kallo ya bi bayan ta kayan da ta sa a jikin ta ya masa kyau matuƙa sai ya gan ta kamar irin kyawawan matan nan da ake tallan sutura da su .( model's ) a hankali ya taka ya bi bayan ta Sofia wacce take zaune ɗim!akan kujera ta kaiwa kujerar wani irin duka da hannu kafin ta toshe bakin ta da hannu wani irin kuka take yi ciki-ciki , irin kishin da take ji a ran ta akan Yakaka muddin bata ɗau mataki ba za ta iya haɗiyar zuciya ta mutu. Lokacin da Doctor Hamza ya idar da sallar Magarib yayi niyyar komawa gida amma yunwar da yake ji da kuma sanin da yayi a gidan ma shi suke jira tunda ya hana ayi girkin sai kawai da ya shigo gidan ya ɗau motar sa ya sake fita ba tare da ya shiga cikin gidan ba . Sofia da ta ji ƙugin tashin motar sa da sauri ta leƙa ta window ta ga fitar sa , tana ganin ya bar gidan a guje ta sauƙa ƙasa kai tsaye ɗakin Yakaka ta tasamma . Tana murɗa ƙofar ta ji a kulle , ɗan kwankwasawa tayi cikin salon da Doctor Hamza yake yi . Yakaka wacce take zaune ta miƙe a hankali ta ƙarasa jikin ƙofar . Haka kawai ta ji zuciyar ta ta doka da ƙarfi dan haka ta dakata ta fasa bude kofar cikin siririyar murya tace "Waye ? Shiru Sofi tayi tana fatan ta buɗe su gamu , sake dukan ƙofar tayi da karfi da hakan ya sa nan take Yakaka ta fahimci wace ce a wajen dan haka a sarari ta furta "Auzu Billah minash Shaytanir Rajeem, baya ta koma ta zauna a inda ta ta shi. "Ya kamata na samarwa kaina da mafita ni Yakaka lamarin Matar nan ya fara wuce iyakata ta musulunci , ta furta hakan a sarari kawo yanzu ta haƙaƙe da gasken gaske sofi ta ɗaura ɗamarar yaƙar ta dalili kawai;sun hada Miji daya. "Ina Mafita? Haka Sofia ta gaji da bugun ƙofar tana surutai , jin shigowar motar Doctor Hamza ya sa tayi saurin barin wajen ta koma ɗakin ta kai tsaye banɗaki ta shiga ta sakarwa kan ta ruwan sanyi . Kusan mintuna goma sha biyar suka kwashe suna jiran sofia ta zo su ci abinci amma shiru ba alamun ta sau uku yana ƙiran layin ta wayar tana ƙara bata ɗauka , Ran sa ya fara ɓaci da salon rainin da yake hango take-taken sa daga Sofia wanda kuma ba zai ɗauka ba . "Wafaa hau sama ki ƙira Sofia . Kamar bata fahimci abunda yake cewa ba haka Yakaka take jahiltar sa da ido . Ganin yadda tayi da fuska ya sa shi miƙewa da kan sa ya nufi saman . Yakaka wacce ta bi shi da kallo da tuno da abunda ya faru jiya daga zuwa ƙiran Sofi ya sa ta miƙewa tsaye da sauri . "yaya Dakta . Ta ƙira sunan sa , a hankali ya waigo. "zan bika . tace tana yin narai-narai da ido . Bai amsa ba sai hannun sa da ya miƙo mata alamar ta taho da sauri ta isa gare shi tana jefa hannun ta cikin na shi , ya riƙe ta suka hau saman tare . Sofia wacce take tsaye a maɓoyar ta tana ganin duk abunda ya faru kafin su ƙaraso ta fito da sauri kamar daga ɗaki ta fito , Wani irin kallo ta watsa musu kafin ta gyara fuskar ta tana cewa " Yaks manya ke dai ko ina kina liƙe da Miji ɗa Namiji daɗi ko ai kin saba . "Sofi sau nawa zan faɗa miki ki daina min yawo a gida tsirara-tsirara ? Doctor Hamza ya katse ta ba tare da ya bari zancen da tayi yayi tasirin da zai hana shi sukuni ba duk da cewa kalmomin ta sun taɓa ran sa . Buɗe baki Sofi tayi cike da mamaki kafin ta mayar da ganin ta kan Yakaka wacce ta sunkuyar da kan ta a tun kallon farko da tayiwa Sofi da take sanye da wasu bodycon sleeve rigar duk bata karasa kugun ta ba wandon kuwa iyakar shi ƙourin ta rashin kaurin da kayan ke da Su ya ya taimaka wajen fiddo da halittun jikin ta . Narke murya tayi cike da kissa tana ƙoƙarin haɗiye fushin ta tace "Doctor kai ne fa kake cewa kafi son kana gani na a haka Kana jin daɗi tare da samun gamsuwar ido sobada ganin ko ina nawa a ciccike ko ka manta ne ? Kai ne fa kake cewa siririyar mace ramammiya haushi take ba.... A hankali Yakaka ta zame hannun ta tayi baya tana barin wajen saboda fahimta da tayi gaba kaɗan Sofi zata ce wani abu da zai fi haka ji mata ciwo . "Duk ban tambaye ki wannan zancen ba dan na lura bakya jin kunyar ƙarya Sofi da girman ki amma ina so ki sani a yanzu ba mu kaɗai ne a gidan dan haka bana so na sake ganin ki haka kina min yawo a gida . "Riga da wondo ne fa Doctor na ? Ta furta hakan a shagwaɓe zuciyar ta sol ganin Yakaka ta ɓace a wajen . "Eh amma na 'yan iska ba ? Ko Wafaa ma ai riga da wondo ta saka amma na mutunci da zata iya fitowa a gaban ki kuma sun mata kyau sun burge ni . "Ki koma ki sauya kaya ni ba zan iya cigaba da jiran ki cin abinci ba zamu fara ci dan yunwa nake ji . Daga haka ya juya yana barin wajen , Sofi ta bi jikin ta da kallo kalmomin sa na dawo mata a kai "Doctor yana daf da kufce min na shiga uku ni Safiya ni ce yau yake cewa na dunga rufe masa jikin da a baya yafi kaunar ganin sa fiye da television? Bayan sun gama cin abincin da Yakaka take jin sa ba wani daɗi sosai hakan kuwa bai rasa nasaba da yadda duk suka haɗa ido da Sofi sai ta galla mata harara . Dan haka tana gama ci ta miƙe zata yi tafiyar ta Doctor Hamza da duk yake kallon motsin su ya dakatar da ita ta dawo ta zauna har ya gama cin abincin sa . Sannan ya fara yi musu nasiha cikin nutsuwa da fiye da rabin ta yafi karkata akan tunasar da su kan gujewa ɗaukar hakkin juna/cutar da juna sannan ya kwaɗaitar da su daɗin da za su ji su kuma jiyar da shi muddin suka zauna lafiya da juna a matsayin 'yan uwa ba abokan hamayya ba sannan ya tunasar da su shi aure bangare ne na ibada da ake samun ɗimbin lada a gurin Ubangiji Allah ta dalilin sa , dan haka yake jaan hankalin su da suyi ƙoƙari wajen ganin sun yi bautar su yadda ya dace. sai ya rufe da cewa "Muddin kuka haɗa kai ku ka min rumfa ku ka bani kariya , ku ka bani kulawar da ta dace da ta samar min da nutsuwa ai ba za ku bar wata damar da wata za ta sake ratso tsakanin mu ba ku biyun nan kun isheni rayuwa ta duniya Safiya da Amina bayan ku duk sauran mata ba zan gan su har su burge ni ba Da murmushi Yakaka take kallon sa kalmomin sa sun mata daɗi sosai kafin a hankali tace "Yaya Dakta da yardar Allah ba zamu zama sanadin tashin hankalin ka ba kai ma ka dunga mana addu'a Allah ya haɗa kan mu ya kori shaiɗan a tsakanin mu . "Ameen Wafaa tun kafin yanzu ina muku addu'a zan kuma cigaba da yi muku insha Allah . "Sofi baki ce kome ba ? Ya furta hakan yana ɗora ganin sa akan ta wacce ta tattara hankalin ta duk akan fuskar wayat ta kamar bata wajen ' Sake yi tayi kamar bata jin sa duk kuwa da cewa sarai tana jin nasa shi ma kuma ya san tana ji dan haka ya ɗauke ganin sa daga kan ta ya mayar ga Yakaka yana cigaba da cewa "Sai batun kwanakin girkin ku bayan kin gama kwanakin ki bakwai na amarci kamar yadda addini ya tanadar da yau kike da kwanaki biyu a gidan nan dan haka yau mun samu kwana biyu ko Wafaa ? Murmushi Yakaka tayi tana gyaɗa kai , a hankali ya miƙa hannu ya riƙo hannun ta da yake ajiye akan teburin gaban su kafin yace "to kwanaki nawa za ku dunga yi na girki kwana ɗaya ko biyu ? Kallon Sofi tayi ta ga yadda ta zuba mata ido ɗauke kan ta tayi murmushin ta bai ɗauke ba tace "yadda duk kake so Yaya Dacta amma ana yin raba kwana ɗayan ne ya zama awanni 12-12 ? Da mamaki tare da zumuɗin son jin manufar ta yace "idan ana yi me zai faru ? A shagwaɓe Yakaka tace " Sai ka dunga yini a sama 12 hours kana saukowa ni kuma mu kwana tare tunda ka ga ni fa ƙarama ce kuma 'yar siririya idan dodo ya zo min da dare ya zan yi ? . Wata 'yar sassauƙar dariyar da take tafe da amon nishaɗi Doctor Hamza yayi kafin ya lakace tsinin hancin Yakaka yace " Wafaa lalle kam ke yarinya ce amma ba'a haka sai dai kwana ɗai-ɗaya ake yi dan haka zan dunga kwana ɗaya a sama ɗaya a ƙasa tare da ke kin ji.. " What the hell ? Dole mana ki ce haka tsohuwar kilaki uwar jarababbu , idan karuwancin kike ji da shi ai da sai ki cigaba da tsayawa a bakin titi kamar yadda kika saba a can ba za ki rasa wanda za ki dunga kwana da shi ba kullum amma tun da kika auri Mijina wal.' "Sofi bana son hauka da rashin tarbiyya a gabana kike zagin ta daga wasa ? .. Doctor Hamza ya katse ta a tsawace . Bata dube shi bare ta yi ko gizau ta cigaba da cewa "Kuma wallahi ban yarda da kwana bakwai ba wannan bazaurar za'a yiwa kwanaki bakwai da ake yiwa budurwa gal a leda ? Daga gobe kwanan ta uku ya ƙare kuma kwana biyu nake son a dunga yi na girkin aikin banza tsohuwar 'yar iska kawai za ki zo kina wani yen-yen-yen wai ke ga 'yar barki to na bi barikin da gudu . "Sofi zan matukar saɓa miki idan kika sake maimaita makamantan kalmomin da kika furta , Wafaa Matata ce ni ne nake auren ta ba ke ba , budurwa ce ita ko ba budurwa ba ce ba hurumin ki bane , A sanina bata taɓa aure ba dan haka a matsayin budurwa na aure ta ko da kuwa ba budurwar bace tsautsayi ya gifta a rayuwar ta kamar yadda na aure ki a matsayin budurwa duk kuwa da ban samu tabbaci kan tsautsayin da .... Wani irin ihu Sofi tayi tana miƙewa tsaye tayi kukan kura ta jawo Yakaka ta cukui-kuye ta bata cikin hayyacin ta take jijjigata "sai kin faɗa min irin asirin da kika yiwa Mijina da tun ranar da ya fara ganin ki ya susuce akan ki tun kina kuchakar ki ƙazama fiye da shekaru shida na zauna a ƙarƙashin mulkin da kike yi a zuci.. "Sofiya ki sake ta , ki sake ta nace kafin na saɓa miki . Doctor Hamza yake furta hakan yana ƙoƙarin shiga tsakanin su ko kusa shi ba mutum bane mai son tashin hankali da hayaniya ga Sofi tana neman dagula masa lissafi ta ko'ina . Ƙarar marin da ya karaɗe wajen ya taho da wani ɗan takaitatcen shiru a bayan sa 'tsit' kamar an kashe radio sai numfashin Sofi da ke sassarfa yana kai kawo lokaci ɗaya idanun ta ke tsartuwar wasu zafafan hawaye da take jin ɗacin su har a maƙoron ta hannun ta ɗaya dafe da ƙuncin ta ta ɗaga ɗayan hannun tana ɗorawa a kirjin ta da wata shaƙaƙƙiyar murya tace "Doctor Ni Ni Ni ka mara ? Jaan numfashi tayi kafin ta juyar da ɗan allin ta kan Yakaka da take laɓe a bayan Doctor Hamza tana leƙen ta tace "akan wannan ka mare ni ? Akan ta ? Ba sabon sa bane dukan mace shi ko hararar Matar auren sa bai cikin tsarin rayuwar sa sai fa da Allah ya haɗa shi da 'yar gagara irin Sofi yasa dole a wasu lokutan yake ɗaga mata muryar sai dai duk da haka a duk zaman su bai taɓa ɗora hannu akan ta ba sai fa yau da ta kai shi maƙura ta gajiyar masa da ruhi da gangar jikin sa sannan kuma tsananin So da yake yiwa Yakaka ya ingiza shi ganin tana neman ji mata ciwo bayan irin kalamai na ɓatanci da take furzo mata da suke tafasa masa rai ' Nadama na son kawo masa farmaƙi ya ɗaga hannun sa yana mai matsawa kusa da ita yace "Mu ga gurin baki ji zafi ba ko ? Ai ke ce kika jawo Sofi . Da sauri ta kauce idanun ta har wani jirkituwa suke yi saboda tsabar tashin hankali da ruɗanin da take ciki. Ta buɗe baki amma ta gagara cewa kome ko'ina na jikin ta tsuma yake kawai sai ta juya da maɗaukakin taku ta bar wajen kamar ana ingiza ta . Da hannun sa ɗaya ya dafe kan sa bayan barin ta wajen gaba ɗaya nadamar ɗora hannu akan ta yake yi ,"Nagartatcen Namiji ba ya dukan Mace , zuciyar sa ke tunasar da shi hakan. waje ya samu ya zauna ya yi tagumi da hannu biyu, Yakaka wacce ita ma jikin ta yayi sanyi akan abunda ya faru duk tana ganin kamar har da laifin ta ita ta tunzura Sofi a ƙoƙarin ta na ganin ta rama wasu kalmomin cin fuska da ta san da gangan Sofia ke furta Su a gaban ta dan ta bata haushi. Durƙuso tayi a gaban sa tana jin tausayin sa na kawo mata "duk ke kika jawo ɓangaren zuciyar ta ya ƙalubanci ɗaya ɓangaren.' "Yaya Dakta kayi haƙuri d.. Shit yace mata yana sauƙe hannun sa ya ɗago ta daga durkuson da tayi ya mata wajen zama akan ƙafar sa idanun sa da suka yi ciki saboda gajiya da damuwa su ya ɗaga yana bin ta da kallo rigar jikin ta duk ta yamutse har ta yage ta wuya saboda cukumar ta da Sofi tayi , idanun sa ya sauƙe a ƙasan wuyan ta kaɗan da duk yayi birɗi-birɗi kamar borin jini . Da sauri ya wara idanun sa kafin ya kai hannu yana janye rigar da hakan ya bashi damar ganin jikin ta sosai, da Sauri a kuma tsorace yake duba sashin jikin ta da gaba daya yayi burɗi-burɗi. "Wafaa wannan anxiety rashes ɗin me ya kawo miki su ? Tsoro ? Tsoron me kike haka ? Wafaa ki rage tsoro ba abunda zai same ki a duk lokacin da kika tsorata da wani abu kiyi addu'a Wafaa . "Kin ga yadda duk jikin ki ya tashi , kin ga duba . Yace yana nuna mata hannun ta da shi ma duk yayi ruɗu-ruɗu . Fuskar ta ya riƙe da hannun sa kafin yace "faɗa min me kike tsoro ? Sauƙe idanun ta tayi kafin a hankali tace "Babu . "Babu ? Ya tambaye ta cike da shakku "Eh . Ta amsa tana miƙewa daga kan shi "yaya Dakta zan tafi na kwanta dare ya fara yi. Taku ɗaya tayi ya riƙo hannun ta kafin ta ankara ya dawo da ita inda ta tashi ya kewaye ta da hannun sa kafin ya kwantar da kan shi a ƙirjin ta yana shaƙar ƙamshin jikin ta yace "meyasa za ki gudu ki bar ni bayan kin san ina da damuwa ? Ba zan ji daɗi ba idan aka ce zaman ku ya zama haka , ba zan samu farin-cikin da Magidanta ke samu a gidajen su ba muddin kuna faɗa . ina tsoron gaba na samu rarrabuwar kai a tsakanin 'ya'yana . Shiru yayi kafin ya ɗago kan sa daga jikin ta da taimakon hasken da yake wajen tar ta iya hango yadda idanun sa suka yi jawur da har sai da tsigar jikin ta ta miƙe . "A gare ki ina zaton zan samu kwanciyar hankali Dan Allah kar ki min bazata kin ji ? Gyaɗa kai tayi duk da bata gama fahimtar kalmomin sa ba ya ɗora da cigaba da cewa "Duk abinda Sofia za ta miki kiyi haƙuri kar ki dunga biye mata kuna tashin hankali fitina ba halin ki bane Wafaa kar ta ɓata min ke . "ke saliha ce managarciya salihar mace irin ki bata tashin hankali duk abinda zata faɗa kar ya tunzura ki har ki biye mata kuyi rigima kin ji ko ? Ya furta hakan yana ƙurewa fuskar ta kallo, ɗago kan ta tayi su ka haɗa ido Kalaman sa sun mata tasirin da yasa ta lumshe idanun ta da wani boyayyan murmushin da ya ɓullo daga can ƙasan ran ta har wani danshi take ji daga saƙon zuciyar ta yana ratsa mata sassan jiki samun yabo a wajen wanda kake neman yarda da amincin sa abu ne mai daɗi da haifar da nishaɗi. ba tare da gangar jikin ta tayi shawara da ita ba sai ta tafi a hankali ta kwanta a jikin sa tana kewaye shi da nata hannun da hakan ya sa shi rufe Idanun sa ya matso da ita sosai jikin sa ya rungume ta . Daɗewa da yayi yana fama da son ta daɗi da yadda yake kan gabar neman mai tallafin sa a dai-dai lokacin da ƙwaƙwalwar sa ke buƙatar hutu sai gangar jikin sa ta mata tarɓa na musamman da ahankali ya fara bin jikin ta da hannun sa ya shiga gwadama mata zallar ƙaunar da yake mata tun a mafarin farko. Tana jikin sa ya miƙe tare da ita cike da gudun abun da zai gifta tsakanin su ya daƙile masa daddaɗar nutsuwar da yake samu a tare da ita da ba zai ce ya taɓa samun makamanciyar ta ba . Washegari a tare suka tashi cike da nishaɗi suna hirar su suka shiga kitchen tare tana girkin ta yana mata hira da tsokanar ta lokaci-lokaci yana ɗan kasa kunne ko zai ji motsin fitowar Sofia amma ko alamar ta babu har lokacin da ya koma ɗaki yayi shirin tafiya aiki ya fito suna shirin fara cin abinci Yakaka ta danne zuciyar ta a hankali tace "Yaya Dakta har yanzu bata fito ba ko za ka kira ta muyi breakfast ? Kallon ta ya yi da yanayi na ko'in kula a muryar sa yace "ita da kan ta za ta fito kyale ta . "Zuba mana abincin mu ci ina sauri Wafaa. Cikin nutsuwa ta zuba musu soyayyan dankalin da ƙwai hadi da soyayyar ayaba , sai kuma farfesun marara zallah da tayi masa dafuwa irin na mutan Ndjamena (shurban) a ƙasa ta ajiye musu abincin a tsakanin su . Suna ci Doctor Hamza yana ta santi , jin sa yake kamar ya dawwama a haka yana kallon fuskar ta da take cike da annuri . Bayan sun gama cin abincin ya goge bakin sa da tissue "Wafaa ya ƙira sunan ta. "Unmh Ta amsa tana ɗago kan ta hannun sa da yake miƙa mata wani kwali mai kyau ta bi da kallo ba tare da ta karɓa ba ta daga idanun ta ta mayar kan sa da sigar tambaya? " karɓi mana , sabuwar waya na saya miki ta hannun ki bata da wani amfani koyaushe na ƙira ba kya ɗauka kamar jiya kam ma a kashe ta wuni , bana jin daɗin haka na fi son na dunga jin ya kike ? Ko da bana gida . Da yalwatatcen murmushi tare da ɗan boyayyen zumuɗi ta karɓi kwalin kafin ta fara kici-kicin buɗewa bai dakatar da ita ba har sai da ta buɗe ta zaro sabuwar waya sumfurin iPhone8+ da take ta daukar ido . "Masha Allah . ta furta a sarari lokacin da take kallon sa with her light brown eyes that were deeply creased with smile line at the coners. "Yaya Dakta Wannan wayar ta 'yan gayu tawa ce? Ta furta hakan da zallar farin-ciki kafin ta ɗora da cigaba da cewa " Kai wallahi nagode sosai , ina nufin nagode dayawa Ya Dakta Allah ya daɗa ma buɗi da arziki mai Albarka... "Wafaaa ya ƙira sunan ta ƙasa-ƙasa yana jin yadda farin-cikin da ya hango tare da ita ya ke ba shi wani shauƙi na musamman Kumatun ta ya ɗan shafa yana miƙewa tsaye bayan ya ɗauki briefcase din sa da murmushi yace " Wafaa I can bring the whole world to you if I have it. A hankali ta dago kan ta rana ta farko da ta ji kamar tana son mayar masa da martanin tsadaddun kalaman sa tana so tace wani abu ko da kadan ne akan tarin alkhairin sa marasa adadi da ya wanzu yana hidimta mata, "to me zan ce ne? Ta tambayi kan ta, daga can ƙasan ran ta kalmomin suka haɗo kan su suka fito ta tsakanin laɓɓan ta ba tare da ta janye ƙwarar idanun ta da ke cikin na shi ba ta ce "I always cherish your company Yaya dakta for that I'll forever serve you and do anything for you here in Duniya insha Allah. Thank you for everything! I mean everything Yaya Dakta. Ɗage girar sa yayi yana jin sa kamar mai yawo a sama kalmomin nata taƙaitattu ne amma masu faɗi ne a wajen sa da zai yi zama na musamman domin yi musu fashin baƙi , " I appreciate that and I cherish yours even more, integrity you're worth-valuing, worth-treasuring and worth-cherishing. Your value is such unfathomable Wafaa. zamewa ƙafar Sofia tayi da ƙiris ya rage ta gangaro daga ƙafar bene, bata taɓa sanin ƙeyar mutum na da ido ba sai da ta ji tana taka matakalar bene ta baya , kalaman na mata amsa kuwwa suna mata rakiya har ɗakin baccin ta da ta na shiga ta zube a ƙasa kan ta na juya mata tana ganin kome na dakin yana tafiya da kafafun sa. A narke Yakaka take kallon sa lokacin da yake furta mata kalmomin da suka mata zurfi wajen fassara har ya sunkuyo ya sumbanci goshin ta, " ni zan tafi Wafaa . Ya furta haka yana ɗaga taku ya nufi hanyar ficewa daga falon har ya kai ƙofa ya waigo ta , kallon sa take da murmushin da yafi so a tare da ita a hankali ya ƙarasa ficewa a falon ran sa cike taf da ƙaunar ta fuskar ta tana zanuwar masa a cikin rai yana jin zata ishe shi farin-cikin yau har ya je ya dawo . Ya tada motar sa a hankali yana ficewa a gidan zuciyar sa na daɗa hasko masa yanayin da ya bar ta a ciki " she's smiley, she is smile just like the sunflower. Ya furta hakan a sarari. Cike da zumuɗi Yakaka ta kunna wayar da cikin sa'a ta tarar da sabon Sim a ciki , duk da bata taɓa riƙe babbar waya ta kan ta ba amma bata gagara sarrafa wannan ɗin ba saboda Lubna tana riƙe irin su a wasu lokutan tana karɓa tayi 'yan taɓe-taɓen ta saboda sosai manyan wayoyi suke burge ta dan dai kawai bata da damar mallakar su ne . Ta kwashe tsawon lokaci tana wasa da wayar cikin taka tsan-tsan ta shiga nan ta fita can kafin ta miƙe tana riƙe da wayar duk hankalin ta na kai ta tafi ɗaki ta ɗauko tsohuwar wayar ta ta kunna ta cike da zumuɗi ta kwafi number Hajja akan sabuwar wayar ta ta fara ƙira da ɗokin son ta yiwa Falmata albishir . Bugu ɗaya Hajja ta ɗaga tana ɗauka da ta ji muryar Yakaka sai ta sa dariya "Ah ka ga manya a baku naku daban Babba Uwar Mama uwargida kuma Amarya a gidan Babban likita , ai yau kwana uku kenan uwarɗakina tana nacin ƙiran wayar ta ki bata samu tun ranar da muka samu labarin kin tare da fatan ana Amarci yadda ya dace ? 'Yar dariya Yakaka tayi ta fara sabo da halin Hajja na jaan zaren magana tayi ta tsawo , "Hajja kenan muna lafiya ya ya wajen ku ? "Mu ma lafiya ras muke bari na miƙawa gimbiyar wayar ku yi magana tana ɗaki . "To Hajja nagode . "Ince da kuɗi a wayar ta ki ? Kar ki katse yanzu zan ba ta A zaune ta tarar da Falmata ta tasa cikin ta a gaba da cikin kwanakin nan yake wani irin girma na ban mamaki daga gefen ta faranti ne a cike da warmers ɗin da aka shaƙe cikin su da kayan cimaka . Miƙa mata wayar Hajja tayi tana cewa "Uwar biyu ma za riƙe waya Babba Uwar Mama ce ke kai . Zunbura baki Falmata tayi kafin ta karɓi wayar tana cewa "Hajja ina faɗa miki bana son sunan nan wai Uwar biyu dan Allah Hajja ki daina . Ta ƙarasa zancen tana kara wayar a kunnen ta dariyar da Yakaka take yi ita ta fara sauƙa a kunnuwan ta da yasa ita ma ta saki 'yar sassauƙar dariyar jin daɗin sauraron tashin muryar 'yar uwar ta da cikin kwanakin nan take jin kewar ta matsananciya . "Yakaka na . Ta ƙira ta da dariya , bata jira ta amsa ba ta ɗora da cewa "wallahi nayi fushi Ya yanyi3 ki ka koma Abuja ba muyi Sallama ba kuma bakya ko nema na yaya Dakta ya mantar da ke ni ko.? Dariya Yakaka tayi tana rufe bakin ta da hannu ta ce "Falmata sharrin da za ki min kenan ? Haba Falmata na tayaya zan mata da ke 'yar uwa rabin jiki , kiyi haƙuri tunda na zo bana cikin kwanciyar Hankali ne Falmata na .... Da sauri Falmata ta katse ta "Yakaka bakya cikin kwanciyar hankali ? Me yake damun ki ? Sofi ce ko ? Me take miki ? "Falmata , abunda Sofi take min ba kyau ta takura min ta hana ni sakewa har fa kare take kawo min cikin ɗaki'....'' "Me ...? Kare ? Falmata ta katse ta hankalin ta a tashe har tana wani ɗan yin zillo da hakan ya jaa hankalin Hajja da take shirin barin ɗakin dan ta basu dama suyi hirar su ta 'yan uwa ta ɗan dawo da baya tana cewa "Uwarɗakina ince dai lafiya ? "Wallahi Falmata kare Sofi ta kawo gidan nan take kulle'.... Chak ta tsaya da bayanin da take sakamakon bugo ƙofar da Sofi tayi ta shigo a haukacen ta daga yadda take gama hanya na nuni da alamun ta shawu . Cikin Yakaka yayi wani ƙugi ƙululu , ba tare da ta katse wayar ba ta sauƙe ta daga kunnen ta ta riƙe ƙam a hannu lokacin da take miƙewa ta tsaya akan ƙafafun ta . Daga can Falmata ta ji shiru Yakaka ta katse zancen da ta faro yi mata zare wayar tayi a kunnen ta ta duba ta ga cewa Yakaka bata ajiye wayar ba , sanya wayar tayi a handsfree da zaton ko network ne da ɗan ƙarfi tace "Hello Yakaka kina jina ? Ki min magana.. Sautin da ta ji ya fara fitowa daga cikin wayar ya sa tayi saƙare tana kallon wayar . "Yakakaakaa ko ? Ko Wafaaaa in Doctor voice ? Ko Aminaa Aminaa , whatever dan ubanki me na faɗa miki akan rayuwa ta da kika shigo kin manta alƙawarin da na miki dan me koyawa tsohuwar ki darasi ? Da har ki ka iya yin tsaurin idon yi min rashin kunyar da ta sa aka mare ni akan ki Kin yi kuskuren da ba zan bari ki maimaita makamancin sa ba . Girgiza kai Sofi tayi kamar lokacin aka mare ta ta riƙe ƙuncin ta "Mari ni Sofi aka mara akan ki.? Taku ta fara yi tana kusantar Yakaka wacce ko ba'a faɗa mata ba ta fahimci manufar Sofi , kuma tuni ta fara neman hanyar tsira . Laɓɓan ta na rawa ta fara jaa baya tana cewa "Anty Sofi Dan Allah kiyi haƙuri walla.'.. Wata waftar da Sofi ta kawo mata ya sa ta daka tsalle ta tsallaka kan gadon ta hau ta tsaya.. "Zan kashe ki Yakaka na ga abunda zai faru ba dai kin gwada min naci ba ? Kin nuna a dole Mijina naki ne ko ? To sai na kashe ki kamar yadda na sha alwashi. Daga can kuka Falmata ta sa ta yunƙura da ƙyar ta miƙe jikin ta na rawa ta miƙawa Hajja wayar da duk abunda Sofi take cewa a kunnuwan su muryar ta na rawa tace "Hajja , Hajja kin ji wai Sofi za ta kashe min Yakaka wallahi kuma za ta iya dan Allah ki bata hakuri Hajja. Karɓar wayar Hajja tayi ta shiga cewa "alo 'Alo babba uwar Mama ba wa mahaukaciyar kishiyar ta ki wayar dan ƙunduƙurin ubata yau ji min tsinannana? Kishi hauka ne? Jin shiru yasa Falmata ta sake rikicewa da muryar da take gaf da fara kuka tace , "Yakaka , Yakaka Dan Allah kiyi magana , Yakaka ki gudu dan Allah kar ta kashe ki.. "Ke jaa can ar kishiyar za ta guduwa ? Zancen banza ma kenan ,mugun nufi ai baya kashe ɗan barewa Babba uwar Mama zage ki taushe bakin akuyar wofi ki ɗaga ta sama ki doka ta da ƙasa kika yadda kika gudu ni da ke ne , nace ki zage ƙwanji 'yar nan ki kwaci 'yancin ki ta isa ne ma ta kashe ki ? Naushe ta a ƙahon zuci nace. Hajja ta furta hakan har tana kaiwa iska duka tana cije baki cike da jin wani irin takaici na rufe ta . Daga can kokawa tuƙuru ta sarƙe tsakanin Yakaka da Sofi da take neman shaƙe Yakaka amma ta kasa samun galaba abun mamaki wani irin ƙarfi ta tarar Yakakan na da shi da ko kusa ba ta yi zaton sa ba dan haka bata ankara ba ta tunkuɗa ta baya bata yi aune ba tayi baya ba shiri daɓas ta zauna da manyan mazauna ta akan wata ƙwalbar turaren da ta faɗo sanadin kokuwar da suke nan take kwalbar tace fusss! Ta fashe a take ta soki ɗuwawun ta. Lokaci ɗaya wani irin raɗaɗi ya ratsa mata ƙwaƙwalwa da yasa ta saki ihu kafin ta dawo hayyacin ta Yakaka da daman matsera take nema ta tsallaƙe ta da gudu ta fice daga ɗakin bata tsaya ba ta buɗe ƙofar falon ta fita daga ita sai kayan jikin ta ƙafar ta ko takalmi babu sai fa wayar ta da take riƙe ƙam a hannun ta . Sofi wacce bata saurari azabar da mazaunan ta ke mata ba ta fito gaba gaɗi tana ganin ƙofar falon a buɗe ta fahimci Yakaka ta fice a gidan abunda daman take so kenan . Dan haka ta tura ƙofar falon da ƙarfi ba tare da ta kulle ba ta juya ta hau sama saboda raɗaɗin da take ji a mazaunan ta tana son ta duba irin raunin da ta ji. Yakaka wacce take tsaye daga harabar gidan ta hango rufo ƙofar da Sofi tayi dan haka a galabaice ta samu waje daga gefe ta zauna baki ɗaya bugun zuciyar ta ba dai-dai yake ba . Sofi ta kulle mata ƙofa ta bar ta a waje da tazarar tsakain ta da titi bai wani cika nisa ba sauran mutanen da suke makwaftaka duk za su iya ganin ta haka babu mayafin kirki wannan wane irin rayuwa ce take yi ? Kiran wayar ta da aka yi yasa ta duba fuskar wayar sunan Hajja ta gani dan haka ta ɗauka tana ɗagawa daga can Falmata da ta kasa zaune ta kasa tsaye ta ce "Yakaka ke ce ? Bata mi ki kome ba ko.? D'' "Falmata ni ce eh na samu na gudo ki....' "Kika gudu ? Gudu fa kika ce ? Hajja take tambayar ta daga can kafin Yakaka ta ce wani abu Hajja ta karɓe wayar daga hannun Falmata tana cigaba da cewa "Ke wacce irin Solobiya ce ? Kishiyar ke bin ki kina rugawa da gudu dan ragwanta da mutuwar zuciya kenan ko me ? Bakya tsayawa ki nuna mata banbancin ƙwarin jikin tsohuwa da na yarinya ? Wai ko ba wannan fantekar matar ta babban likita me jemammiyar fuskar nan ba ce ? Yanzu ita kike gudu ? Ita kike tsayawa tana cashe miki haka ba ki rama ba ? to wallahi kin rako mata 'yar nan ah lalle fa kina ina yanzu ? A sanyaye Yakaka tace "ina waje harabar gidan Hajja ta koro ni wallahi tsoro nake ta ɗau wuƙa ta soka min dan haka ta ce min wai wallahi za ta kashe ni kuma ni wallahi bana son tashin hankali Hajja ni fa ko musu na fatar baki ciwon kai yake saka ni bare danbe hajja.... "A ah ai fa lalle abun nayi ne wai an biyawa bazaura Hajji , na gani na kuma shaida haka waliyya to kina jina ko ? "Ba dai ita ta ce 'yar iska bace? Zata hana ki rawar gaban hantsi ke da gidan Mijin ki da ke kuma ta same ki solobiya kike biye mata ? "Hajja ..... "Yi min shiru 'yar nan barni da ita ke dai bin umarni ne na ki , ince dai can layi ta koro ki ? "Eh Hajja . "Da mutane a wajen ko kuwa ? "Eh da mutane dai kaɗan . "A yaya kika fito titin ? Yakaka ta ɗan yi jim ita fa bata cika son biyewa subaɗaɗin Hajja ba muryar Hajjan ta katse ta da ta ji tana sake cewa "Nace da kayan arziki a jikin ki ko kuwa ɗan diras ne a jikin naki ? "Hajja da kaya a jikina . "To yaga su "Eh Hajja? "Nace ki yage kayan ki musu mummunan yagu . "Haba Hajja ya kuma za ki ce ta yaga kayan ta a waje fa take ? Falmata ta furta hakan tana zaro ido da mamaki " kar ki katse ni ki min shiru '. "Babba uwar Mama kina jina? "Ina jin ki Hajja ki saurareni da kyau 'yanci nake son taya miki ki kwato , shi maganin biri karen maguzawa dan haka duk abinda nace miki kiyi , kiyi kawai ina mai tabbatar miki daga yau bata sake chakumar ki da dambe bare har ta kora ki layi . "Ince kina da layin wayar shi Hamzan ? "Ina da shi Hajja " You katse ƙiran nan ki ƙira shi ki tabbatar kina gunjin kuka za ki ƙira shi kice ya taho yanzu ga matar sa za ta kashe ki kina faɗin hakan idan kin tabbatar ya ji sai ki kashe wayar daga nan ki sake ƙira na. Doctor Hamza ya gama round kenan misalin sha biyu saura ya ga ƙiran Yakaka , fuskar sa cike da annuri ya ɗaga ƙiran yana jin 'yar guntuwar gajiyar na barin jikin sa . Sai dai me ? Muryar ta da ya ji cikin kuka ya sa zuciyar sa yin tsalle hankalin sa a tashe yake tambayar ta me ya faru ? Tana kuka ta fara masa bayani bai gama saurara ba ma ya katse wayar hankali tashe ya fara ƙoƙarin barin asibitin . Yakaka tana sauƙe wayar ta ƙira Hajja da daman tsumayar ta take dan haka nan take ta ɗaga "na ƙira shi Hajja . Ta ce a sanyaye . "Yauwa ta farka rigar ta ki ta waje-wajen wuyan sannan ta ƙasa ma ki yiwa zanin naki ko siket mummunan yagu ta wajejen cinyar kina jina ? "Hajja dame zan ya ga ? ba zai ji daɗi ba idan ya gan ni haka jiki a buɗe a waje . "Kin ci gidan ku ana son ƙwatar miki ƴanci kina gardama cewa nake fitinannar matar sa ta koro ki ? Yi maza ki yage kayan nan dan a kori gaba . Ba yadda Yakaka ta iya haka ta ɗan yiwa kayan jikin ta rauni da ƙyar saboda ƙarfin su . Hajja tana iya jin ƙarar ɓarkewar kayan tace "Yauwa to sai abu na gaba da kin dai-daici ya kusa zuwa ki cisge ɗankwalin kan ki ki yasar , kuka kuwa kar ki ƙaƙƙauta har sai kin ga nata hawayen ita ma ba dan kome nasa kiyi haka ba sai dan a kori gaba kin fahimta ko.? "Naji Hajja . "Madallah. Ba'a rufa mintuna goma ba sai ga Doctor Hamza a guje da motar sa da Yakaka tana hango shi ta fara kukan da daman yana cin ran ta kan irin tozarcin da Sofi ke mata. Ƙafafun sa kamar ba za su iya ɗaukar sa ba ya fito a motar idanun sa da suke bayyana tashin hankali akan ta yana bin duk saassan jikin ta da kallo . Yana ƙarasowa Yakaka ta faɗa jikin sa shi ma ya riƙe ta gam da wani irin yanayi a muryar sa yace "wa ya mi ki haka ? Tana shiƙar kuka tace "auntie Sofi . Hannun ta kawai ya kama suka nufi ƙofar shiga gidan yana murɗawa ya ji ta a ɓude ' "Sofi Wacce take baje akan kujera tana zuƙar shisha daga ita sai 'yar doguwar rigar shan iska gefen ta Sam ne a kwance daga ƙasa ta tasa masa abincin sa a gaba yana ci .( irin ita Bosslady ) Lokacin da ta ɗago kan ta tayi zaton Yakaka ce sai kawai tayi ido huɗu da Doctor Hamza da yake tsaye yana mata wani irin kallo na tsana daga bayan sa kuwa Yakaka ce take rakuɓe . Assalam Alaykum masu karatu da fatan alkhairi. Ina dai neman afuwar ku yau da gobe ta fi ƙarfin wasa jiki kuma da jini . Ina kaunar ku domin Allah.' Nagode [4/15, 8:07 PM] +234 706 503 6187: MAFARI ......... HARGITSIN RAYUWA UMM' MUAZ 54 MAI RABON SHAN DUKA Ganin irin mummunan kallon da Doctor Hamza yake yi mata bai karya guiwar Sofi ba da zai sa har ta gaza yin wani yunkuri kare kanta ba . Dan kuwa zuruf ta miƙe bayan ɗan taƙaitatatcen tunanin da ya gifta mata da bata yi ƙasa a guiwa ba ta fara ƙoƙarin tattaro nata makaman yaƙin "ai ba zata bari Yakaka ta ci ta da yaƙi ba haka nan take .ta aiyana hakan a zuciyar ta "Doctor ka ga'..... Wata irin tsawa Doctor Hamza yayi da ba ita Sofi kaɗai ba ,hatta Sam sai da yayi zillo yana ɗan kuka ya koma bayan kujera ya laɓe. "Kar ki ce min kome Sofi , bana buƙatar jin ƙaryar ki ta banza abunda nake so kawai shine ... Ɗan jim yayi yana kallon ta yadda ta wani irin saƙare cikin rashin madafa matsanancin tashin hankali gami da wani nisassashen yanayi shimfiɗe akan fuskar ta inda take bata motsa ba , ba domin tazarar dake tsakanin su na da ɗan yawa ba da babu abunda zai hana ya iya jin sautin bugun zuciyar ta.. "Ki tafi gida Sofi . Ya ce da wata irin kakkaurar murya yana ɗauke ganin sa daga kan ta ya zagayo da Yakaka daga bayan sa yana sake bin jikin ta da kallo kamar dai yana yiwa Sofi nuni da mummunan laifin da ta aikat ,yana kallon fuskar Yakaka tamkar ita yake yiwa maganar ya ɗora da cewa. "Ki je gida akwai buƙatar ki sake samun ƙarin tarbiyya irin ta masu hankali da cikakkiyar koyarwar Islama ko ɗaya ba zan iya sake jimirin ɗaukar salon haukar da kike yi ba . "Ki tafi gidan ku Sofi. Ya furta hakan da buɗaɗɗiyar muryar da yasa kuka tahowa Yakaka da sauri ta shige cikin jikin sa tana zagaye shi da hannunwan ta , matsanancin tsoro na ɗarsuwa a ran ta ganin ɓacin ran sa Mai tsanani irin wanda ta daɗe bata gani ba. "Ga Sofi kenan  matar son sa da ita ce ta kora ta layin. ina ga ita kuma ? Da ta yaga kayan ta da kan ta ? Watakila idan ya gama da Sofi  ya dawo kan ta "shikenan Hajja ta jawo mata . Hannun sa da ya sauke a bayan ta yana ɗan buubbuga ta alamun rarrashi yasa ta ji nutsuwa ta fara dawo.mata da sauri ta ɗago kan ta tana kallon fuskar sa da shi ma ita yake kallo. Zata yi magana ya hana ta ta hanyar jaan hannun ta zuwa hanyar ɗakin sa ba tare da yace  ƙala ba A ɗan tsorace ta dubi sashin Sofi har lokacin tana nan a tsaye inda take tamkar an dasa ta kallo ɗaya ta yiwa fuskar ta tayi saurin janye idanun ta tana jin yadda zuciyar ta ta doka da ƙarfi babu shakka ta hango wani lamari mai kaifi daga cikin idanun Sofi da suka tara ruwan hawayen da basu kai ga zuba ba ' "Ki tafi tare da dabban da kika kawo min gida bana so na fito na ga ɗayan ku . Doctor Hamza ya furta hakan kafin su kai ga shiga ɗaki. Wani irin tsuma jikin Sofi yake so take Allah ya kawo wani ya wanka mata marin da zai farkar da ita daga mummunan mafarkin da take yi "Doctor Hamza ne da kan sa yau yace ta fita ta bar gidan sa ? Razanar da ta tsinka mata gudun jikin jikin bai wuce dalilin korar ta ta ba " akan wannan kuchakar 'yar gudun hijirar  'Yar talakawa 'yar ƙauyen ne Hamzan ta ya kore ta? Kai ina ƙarya ne lokaci yayi da zata farka daga gyangyaɗin da take yi da har yasa tayi saken da wankin hula ke shirin kai ta tsakar dare akan Yakaka. Ihu take son kurmawa amma tana ganin a halin da take ciki babu lokacin ihu , da gudu ta taka ta hau sama ɗakin ta mukullin motar ta kawai ta ɗauka sai fa wani siririn mayafi da ta rufa akai ta fita daga gidan . Wani irin gudu take yi a kan titi da ya zarce ka'ida tana yi tana dukan kan ta da hannun ta ɗaya . Lokacin da ta shiga gidan su kai tsaye falon Momy kori ta zarce wacce bata san da shigowar ta ba sai da ta ji ana mata rotse a falo ta yunƙura daga kwanciyar hutun da take yi akan gado ta fito tana cewa "meye haka ? Meke...' Sauran kalmomin sun maƙale ganin 'yar ta Sofiya ce take mata wannan aika aikar duk ta farfasa mata show-glass Da gudu ta ƙarasa tana riƙo ta Amma sofi sai sake fisgewa take da alamun fitar hayyaci a tare da ita . Hankali tashe take kiran sunan ta "Sofi , Safiya ke Safiya meye hakan ? Kin yi hauka ne dan ubanki.?  Nace hauka kike ? Ganin taƙi saurararta yasa Momy Kori ta cire hannu ta wanke ta da marin da yasa Sofi wani irin juyowa a fusace ta tunkuɗa Momy kori tayi zaman dirshan a kujerar gefen ta . "Momy ki rabu da ni wallahi sai na tarwatsa rayuwar Yarinyar nan yadda nake tarwatsa wannan show-glass din naki. "Wallahi sai na kashe ta , kafin ta kashe min aure ta raba ni da Hamza a ƙarshe tasa baƙin-ciki ya kashe ni . Wani irin kallo Momy kori take bin ta da shi da yake nuni da zunzurutun takaicin da take ciki da kyar ta buɗi baki ta ce . "Yanzun nan ke dan Ubanki akan kishiya kike wannan haukar ? Akan kishiya kika min wannan ɗanyen aiki ? Kika min wannan ɓarnar Sofi ? To billahil azim sai kin biya kuɗin abubuwan duk da kika rotsa dan buhun ubanki. Miƙewa tayi tana jin gara ta bar gurin kafin zuciya ta ciwo ta ta jawo ta ta fara kirɓa . Tana barin wajen Sofi da take tsaye ta silale jaɓar ta zauna a ƙasa kafin ta saki wani irin ihun da farkon sa kururuwa kafin ya miƙa da wani irin Kukan da yake siƙewa ta maƙollotan ta . ...[4/15, 8:07 PM] +234 706 503 6187: MAFARI .......HARGITSIN RAYUWA Umm'muaz 54b Ta ɗau tsawon lokaci a haka kafin ta ji hannun ya dafa ta da sauri ta ɗago kai cike da zumuɗin son ganin Doctor Hamza ne ya zo rarrashin ta . wacce ta gani yasa ta saurin kawar da kan ta tana turo baki gaba . Momy kori ta ƙarasa zama akan kujerar dake daf da ita tana jin tausayin 'yar ta na daɗa mamaye ta shi so jarabbata ne sannan muddin idan Sofi ta gado ta wajen matsanancin kishi to fa tana iya hasashen irin ciwon da take ji a rai wanda ita ma da a ba ita aka yiwa kishiyar ba amma tunda aka yiwa Sofi take cikin jin takaici a duk lokacin da ta tuno . "Sofi kukan nan ya isa haka ki nutsu ki faɗa min me ya faru ?  Ki min bayani dan na cire ki daga wannan halin sanin kan ki ne ba zan juri ganin ki haka ba . Ganin Momy kori ta ɗan sauko yasa Sofi gyara zama ta shiga rattaba labaran da suke cike da ƙarairayi kan irin tozarcin da Yakaka take sa wa Doctor Hamza na yi ma ta tana yi tana sharar ƙwalla a ƙarshe kuma ta juya baya ta kwaye rigar ta ta nunawa Momy kori inda kwalba ta yanke ta tana cigaba da cewa . "Wallahi Momy kin ga inda ta sa wuƙa ta soki bayana kawai dan ta ga yana ɗaukar hankalin Doctor , da kokuwa fa ta kama ni tuƙuru Momy  .... "Dan Ubanki ni rufe min baki ke kina me har wannan afiruwar yarinyar me kama da kazar mayu zata kama ki da kokuwa bakya shaƙe shegiya ki mata ƙamshin mutuwa ? "Amma kuwa albasa bata yi halin ruwa ba cewa nake da wayon ki sarai a gidannan kin san dai kishiyoyi uku na kora idan aka haɗa da wanɗan da zamanin ku na ƙanana kuwa su rai takwas ne ras ai ni bana barin kishiya ta rufa kwana arba'in nake saita mata hanya ko tafi kuturwa naci kuwa. "Amma shine ke dan sakarci za ki sakarwa kishiya baki har ta raina ki tana rarumar ki da kokawa kamar wata sa'ar ta ? Gaba-gaba kuma ai sai dai ta zane ki da bulala, dan ubanta da za ta ce ba za kiyi kiwon kare ba gidan na uban ta ne ko na uwar ta ? "Shi kuma Hamzan da yake ya zama shanyayye sallamamme shine har zai koro min ke yace ki fita ki bar masa gidan ? To bai isa ba ,  Ai auren ku ke da shi mutu ka raba tunda ya zama sanadin da kika je kika huh-hura jikin ki haka kika yiwa kan ki illa ai kuwa bai isa sakin ki ba muddin ina raye ubansa ma na raye . Langaɓe kai Sofi tayi tana kif-kifta ido irin ta wanda gaskiya ta yiwa yawa yake kuma buƙatar a bi masa kadu . Kwafa momy kori tayi kafin ta buɗe murya tana kwala kiran mai aikin ta "Lami ke Lami wai bakya ji ne ? miƙo min wayata ki kuma zo ki tattara gurin nan ki gyara mayyar TV ke da bakya gajiya da kallo sai ki tashi daga gaban Tv haka ya isa . Da gudu wacce aka ƙira da Iyami ta miƙo wayar ta kuma dauƙo tsintsiya ta fara aikin gyaran gurin . Layin Doctor Hamza Momy Kori ta shiga nema amma har ta tsinke bai ɗaga ba , a ƙufule ta sake ƙira wannan karan ma sai da ta kusa tsinkewa Yakaka wacce take gyaran ɗakin inda su ka sha kokuwa ita da Sofi ta ɗaga wayar ganin mai ƙiran "Momy ne kawai a rubuce dan haka tayi zaton Amnee ce . "Hello tace da 'yar muryar ta mai sanyi . "Tsam Momy Kori tayi tana sake samun tabbaci kan duk abinda Sofi ta faɗa mata jin Yakaka ce ma ta ɗau wayar Hamzan lalle Yakaka ta riƙa . "Dan Ubanki ina mai wayar yake ? Ko nima iskanci za ki min ? To bari ki ji ko karuwar uwarki Mayya bata Isa bare ke Dallah ni ba shi wayar nace . Ta ƙarasa tana sakarwa Yakaka wata tsawar da ta razana ta ba shiri ta sauƙe wayar ta ajiye dai-dai da shigowar Doctor Hamza wanda ya sha artabu da Sam kafin ya fitar da shi daga gidan . Yana shigowa wayar ta sake ɗaukar kiɗa ya ƙarasa ya ɗauka ganin mai ƙiran na sa ya sa shi yin tsaki a sarari , har wayar ta tsinke bai ɗaga ba . Nan take wata ta kuma shigowa. "Yaya Doctor ka ɗauka Dan Allah . Ta furta hakan tana ƙoƙarin barin ɗakin hannun ta riƙe da sharar da ta tattara na fasasshiyar kwalbar . "Salamu Alaikum Momy kori . Muryar sa babu walwala ya furta hakan bayan ya ɗaga kiran . Momy kori bata amsa sallamar ba illa tambaya da ta ɗora masa . "Hamza me yake faruwa Sofi ta zo gida haka tana kuka jikin ta jina-jina . Ɗan jimm yayi lokacin da wani ɗan guntun tunani ya gifta masa "jikin ta jina-jina to hatsarin mota tayi ? . "Lafiya ta bar nan kuma ni nace ta tafi gida , Momy kori Sofi ta zauna a gida zuwa wani lokaci ayi amfani da lokacin wajen ƙara mata tarbiyya da tunasar da ita darajar aure da ni kaina idan lokaci yayi zan zo . Jin yana ƙoƙarin ajiye wayar yasa Momy Sofi da take ƙoƙarin danne ɓacin ran ta ta tunzuro dan haka a fusace ta ce "Kai Hamza bana son rashin kunya za ka faɗa min abinda tayi da yasa ka koro ta gida ko kuwa ban Isa ba? "Abubuwan da Sofi take yiwa Amina dayawa har fa kama ta take da kokuwa tana yaga mata kaya sannan ta kora ta layi yanzu wannan dai-dai ne ? "Kana nufin akan matar ka ka koro ta ? To a dalili da me ? Ba ita ta tarar da ita a gidan ba ? Ai ita ya dace ta fita ta bar gidan tunda zaman nasu ba zai yi daɗi ba bafa na son ka fara da rashin adalci . "Momy kori ni kaina Sofi tana min rashin kunya sannan fa har kare Sofi ta ɗauko ba da izinina ba ta kawo min shi cikin gida.. "To shine me ? Ina cewa dai tunda ka san Sofi ka san ta da ƙaunar pets ? .. "Amina tana da Cynophobia ba zai yiwu su rayu gida ɗaya ita da kare ba hakan hatsari ne ga lafiyar ta dan haka Sofi ta cigaba da zama a gida har sai na samu damar raba musu wajen zama . "Rufe min baki sakare idan ita 'yar gwal ɗin taka Cynophobia ne da ita ita kuma Sofi Nostophobia ne da ita haɗi da Zelophobia dan haka tun wuri ka zo ka ɗauke ta ku koma ... Bai ƙarasa jin bayanin ta ba ya katse wayar sa gami da latse ta ya kashe gaba ɗaya . "Ba zan dawo da Sofi ba har sai ta gane kuskuren ta . Ya furta hakan a sarari yana fita falon inda ya tarar da Yakaka a zaune kan kujera ta rafka tagumi duk jin ta take wata mai gagarumin laifi gani take ita ta jaa aka kori Sofi. Zama yayi a daf da ita kafin ya sa hannun sa ya ɗauke hannuwanta da tayi tagumi da su , ya runtse su cikin nasa hannuwan yana ɗan murza mata kan yatsun ta ' A hankali ta ɗago tana kallon sa da ya zuba mata nasa idanun da ke aika mata saƙon zallar ƙaunar ta . "Bana so na ga kina damuwa Wafaa idan ina nan babu mai iya cutar da ke ba tare da na baki kariya ba . Haɓar ta ya ɗan ɗago da hannun sa guda cikin taushin murya ya cigaba da cewa "babu kare yanzu a gidan nan dan haka babu sauran wani tsoro ki saki jikin ki , nan gidan ki ne kin ji ko Wafaa ? Gyaɗa kai tayi kafin a hankali ta motsa laɓɓan ta "Yaya dakta dan Allah Sofi ta daw..'' "Shitt yace yana ɗora yatsan sa ɗaya a kan laɓɓan ta , Shiru tayi tana ɗaga kallon ta zuwa cikin nasa idanuwan da suka ɗan yi ciki kaɗan lokaci guda gangar jikin ta na sauyawa kan irin salon da yake yi da ɗan yatsan sa akan laɓɓan ta. Kasa jura tayi , babu zato ta faɗa jikin sa tana kwantar da kan ta a ƙirjin sa wani irin yanayi na bin jikin ta lokaci ɗaya da wata matsananciyar kunyar sa da bata san ma daga ina ta taso ba mene ne kuma takamaimai dalilin ta. Murmushi yayi mai sauti fahimta da yayi tarkon da ya ɗana mata ya kama ta "ashe ma raguwa ce " ya furta hakan daga can ƙasan ran sa . Ya ɗan ɗauki lokaci da ita a jikin sa alhalin bai mata kome da ya wuce shaƙar ƙamshin humarar ta Mai sanyin ƙamshi har lokacin da ta dawo dai-dai dan kan ta ta ɗaga shi tana sunne kai . Yadda take yi ya ba shi dariya dan haka ya ɗan saki sassauƙar dariya lokacin da yake miƙewa tsaye yana duban agogon hannun sa yace "Wafaa ni zan koma office sai bayan magarib zan dawo ki rufe ƙofar please kowa ya buga kada ki buɗe har sai idan ni ne , kuma ki bar wayar ki a kunne zan dunga kiran ki kin ji ko ? "To Yaya Dacta . ta ce haka tana miƙewa ganin ya fara tafiya , har bakin ƙofa ta raka shi tayi tsaye kan ta a sunkuye tana jiran ya wuce ta rufe ƙofar jin shiru ya sa ta ɗago kan ta bata ankara ba ta ji ya haɗe fuskokin su waje ɗaya tsawon minti ɗaya da 'yan wasu daƙiƙoƙi kafin ya jaa baya yana mata murmushi . Yana wucewa ta rufe ƙofar da sauri tana sauƙe ajiyar zuciya ta jingina bayan ta da ƙofar tana ƙoƙarin daidaita numfashin ta . Har lokacin da ta ji tashin motar sa sannan ta bar wajen ta dawo falo . wani irin nishaɗi take ji yana bin sassan jikin ta da yasa ta yin ɗan wani juyi kafin ta faɗa kan kujera wayar ta dake ajiye a gefe ta ɗauka kai tsaye ta danna ƙiran layin Falmata *** Daga can Falmata ta ɗauka da daman har kawo lokacin hankalin ta bai gama kwanciya ba dan ma dai Biyamuradi ya zo gefen ta da salon kulawar sa gami da ƙaunar sa mai samar mata da nutsuwa . "Hello Yakaka na ta furta hakan cike da zumuɗi a hankali Biyamuradi da yake matsa mata 'yan yatsu ya ɗago kan sa yana kallon fuskar ta da tayi ɓul-ɓul daman bata cika tsawo ba sai ta sake yin round . Baya jin abunda Yakaka take faɗa mata amma daga yadda take ƙyalƙyala dariya ya fahimci labarin da take bata na ban dariya ne wanda irin sa daman aka fi so ta dunga samu a irin halin da take ciki . Dan haka ya ji daɗi a cikin ran sa Murmushi yayi yana miƙewa kafin yayi taku ɗaya ta riƙo hannun sa ɗan tara kumatu tayi alamun bata so ya tafi duk da cewa bata yanke wayar ba . Komawa yayi ya zauna yana rungumo ta ta kwantar da kan ta a ƙirjin sa tana juya harshe cikin yaren su suka cigaba da hirar su ita da Yakaka . Bai katse ta ba har sai da ta gama a hankali ta dago daga jikin sa "Mon bonheur ina za ka tafi ka bar ni? Murmushi yayi yana kallon ƴar fuskar ta yadda ta shagwaɓe fuskar ta masa kyau kamar wata 'yar baby . Kumatun ta ya ɗan shafa kafin yace "Mon bébé kin sani ai bani iya barin ki ko na matsa sai dan watta larura mai girma kouwa . "Kamar wacce irin larura ? ta ce tana ɗaura hannun ta akan nasa . "Kamar ta aiki na Mon bébé. Nan take ta kwaɓe fuska walwalar ta kuma duk tayi ƙaura ita kam bata ƙaunar wannan aikin na Youssouf aikin da zai raba tsakanin su a dai-dai wannan lokacin da take tsakiya da buƙatar sa ya kuma riga ya shagwaɓa ta da zallar ƙaunar sa mai sanya ta jin kamar tafi kowacce mace sa'ar samun Miji a duniya. Sai ga shi lokaci ɗaya zai tafi ya yi mata nisa zuwa wata jahar guda da ta san kome son ta da ganin sa dole ta haƙura da ganin sa kullum kamar yadda yace mata dai idan sun tafi a gobe duk sati zai dunga zuwa ganin ta har lokacin da zata haihu ta gama wanka . Bata san hawayen ta na sauƙa ba sai da ta ji hannun sa mai ɗumi yana shafe mata fuskar ta , Kukan da bata shirya masa ba shi ya taho a lokacin , cikin 'yar muryar ta ta shiga rera kukan da yake sukar zuciyar Youssoufa nan take ya ruɗe ya shiga rarrashin ta ba ita tayi shiru ba sai da ya rufe bakin kukan nata . "Fatima kamar gobbe ne idan na tai sati guda za tai na zo na diba ku kedda ɗiyana kukan ki tada min da hankali yake ko kouwa kina so na bar aikina ? A hankali ta girgiza kai tana ƙoƙarin danne damuwar ta ta ɗago kan ta muryar ta a shagwaɓe tace "amma ka min alƙawarin kullum zan dunga ganin ka a Appel vidéo ko ? "Na miki wannan alƙawarin Bébé duk na samu lokaci zan ƙira ki Appel vidéo ina ganin huskar ki mai haske . Ya furta hakan tare da sumbatar goshin ta . Ƙwanƙwasa ƙofar da aka yi yasa suka gyara zaman su sannan shi yayi iznin da a shigo . Ɗaya daga cikin bayun sashin ta ne take neman iznin shigowa da saƙo daga Hajiya Umma nan take Biyamuradi yayi mata izni Bayan fitar ta suka dawo tare da bayu mata biyu da suke riƙe da wasu manyan farantai da suka sha lulluɓi da wani kyakkyawan tuma-ƙasa da bai ɓoye kyaun kwanukan da suke jere bisa farantan ba . Bayan sun ajiye suka yi gaisuwa sannan suka ɗora da cewa "Saƙo ne daga jagorar cikin gida cewa a kawo wa Gimbiya Fatima . Kamar kullum bayan fitar su Youssoufa da kan sa ya taso ya bubbuɗe kwanukan da suke maƙare da cimaka na alfarma da yafi ƙarfin cin ƙatti goma ma bare fa Falmata da Hajja kaɗai . Yana murmushin da yake bayyana farin-cikin da yake ciki ya dubi Falmata wacce itan ma shi take kallo tana jiran ya zubo mata abincin da jin ƙamshin sa kaɗai duk ya bi yasa yawun ta ya tsinke wata bijirarrar yunwa kuma ta fara sasuƙar ta da yasa ta tuno da rabon ta da abinci tun tattaciyar madarar da ta sha da safe bata ci wani abin kirki ba ga shi yanzu gefen azahar . "Fatima kin zama 'yar gatan Umma kullum cikin kwasar gara kike bayan saƙonni gaisuwa da girmamawa da suke isko ki a kullum anya kouwa baki haye min ƙaraga ta ga wajjen ta ba ? Dariya tayi har gajerun haƙoran ta na bayyana kafin ta ce " ai kada kayi kokonto Biyamuradi yanzu ni ce ke da Umma . Yunƙurawa tayi zata miƙe da sauri ya taso ya kama ta suka tako tare zuwa gaban abincin bayan ta zauna ya jingina mata pillow daga bayan ta tana ɗan sake bajewa . Da hannu take gwada masa waɗanda take so yana zuba mata , lokacin da ya gama wani cokalin daban ya ɗauka zai bata a baki fahimtar hakan da tayi yasa ta karɓe plate ɗin daga hannun sa da sauri ' ba zata iya jurar yunwar da take ji ba , bare har ta iya jira a ciyar da ita bayan tayi Bismillah cikin nutsuwa ta sanya hannu ta ta fara ci . Daɗin abincin na ratsa ta yana dasa mata ƙaunar uwar Mijin ta da ta fahimci tunda abun nan ya faru ya wuce baki ɗaya ta sauya duk wata rashin kulawa da rashin ƙaunar da take gwada mata sun juye sun rikiɗe sun koma tsantsar kulawa da nuna ƙauna a fili . Tun faruwar lamarin da rashin lafiyar da tayi har ta samu sauƙi cikin sati guda kuma ta tare a sabon sashin ta da ta zo ta tarar da shi a shirye tsaf cike da kayan alatu irin na saraki da Biyamuradi ya tabbatar mata da cewa Maimartaba ne ya mata kome har sai da tayi hawaye cikin ran ta kuwa ta dunga miƙa godiyar ta ga Allah da idan ba shi ba babu mai ɗora misuƙa miskiniya irin ta a matsayin da take a yau babu shakka Allah shine abun godiya . Bayan Hajja da take taya ta zama an haɗa ta da bayu mata biyar masu hidima kaɗai a sashin ta duk da cewa ba girki suke mata ba sai fa aiyukan shara da goge-goge ,wanke-wanke da sauran ƙananun aiyuka . Abincin ta daga Sashin Hajiya Umma yake tahowa ita ta hana ta cin kowanne abinci sai fa na sashin ta har zuwa lokacin da zata haihu sannan ta sauwaƙe mata zuwa gaida ta kullum ta ce ta dunga sanya kwana ɗaya a tsakani saboda tayi nawi kuma da 'yar tazara a tsakanin su Hajja ita ke zuwa kai gaisuwa kullum. Tana tunanin zuci bata san ta cinye abincin ba sai da ta laluba ta ji ba kome sai 'yan tsirarun shinkafa. Ta ɗago kan ta a hankali ta dubi Fuskar Youssouf wanda ya rafka tagumi da hannu biyu yana mata kallo mai ruwa biyu , zallar ƙaunar ta da kuma tausayin halin da take ciki . A kunyace ta ɗan yi murmushi kafin tayi magana ya riga ta da cewa "kin ƙoshi ? Bai  jira amsar ta ba ya kai hannun sa ya goge mata gefen bakin ta da miya ta ɗan sauƙa. "Mon Bébé kin ƙoshi ? Ya sake tambayar ta " Na ƙoshi Baban Mama ta furta tana ƙoƙarin tashi shi ya taimaka mata ta wanke hannun ta . Tare suka zauna yana maƙale da ita ko yaya ta motsa yana mata sannu tare da gwada mata So. ƙiran Sallah da akayi shi yasa shi sallama da ita bayan ya fita kai tsaye sai da ya shiga sashin Siyama da tun asuba rabon shi da ita saboda girkin Falmata ne A zaune ya same ta an yi mata zanen ƙunshi a fararen ƙafafun ta tana jiran ya bushe ta wanke . Daga inda yake yana iya hangen jelar ƙananun kitson da aka mata da suka kwanta har a kafaɗun ta 'yar doguwar fuskar ta ta sake fitowa sai ƙyallin gyaran jikin da ta samu take yi . Ba tare da ya zauna ba yake amsa gaisuwar da Siyamar ke yi masa bayan sun gama gaisawar ya ɗan yi murmushi kafin ya ce "wannan ƙwalliyar du ta tafiyar ce ? Ko kouwa tawa ce ? Ɗan wara idanun ta tayi sai kuma tayi dariya cike da jin daɗi da ɗoki ta ce "ƙwalliya taka ce Baban Yumna kamar yadda tafiyar ma take taka domin kai . Ɗaga mata gira yayi yana juyawa akan ƙafafun sa yace "idan hakka ne ayi shiri da kyau a kouma gama bisa kan lokaci doumin kamar yadda na faɗi gobbe kafin hantsi ya ɗagga zamu tai da yardar Allah . "To Insha Allah ba zan makara ba. Ta furta hakan tana bin bayan sa da kallo wani irin farin-ciki na ratsa ta sanin da tayi gobe iwar haka daga ita sai shi a wani yanki . Daren ranar kusan raba shi suka yi Youssoufa yana aikin rarrashin Falmata da shima kawai daurewa yake yi amma har cikin ran sa yake jin rabuwar da zasu yi. Dan dai babu yadda zai yi ne a cikin halin da take ciki ba zai yiwu ya ɗauke ta su tafi bariki ba can wata jahar da babu kowa nasu ko shi da kansa ba zai so hakan ba bare ma kuma Hajiya Umma da Maimartaba sun riga sun gama magana akan ya bar ta anan gida har ta haihu abunda ta haifa yayi ƙwari kafin ta fara bin sa jahar da yake aiki . **** Washegari. Duk yadda Falmata ta so ta ɓoyewa Siyama damuwar ta lokacin da ta shiga sashin ta domin yi mata Sallama kasawa tayi . Idanun ta suka tara ruwan hawayen muryar ta na ɗan rawa tace "Maman Yumna zan yi kewar ku ke da Yumna sosai dan Allah ki dunga ƙirana Appel vidéo . Riƙe hannun ta Siyama tayi cikin ran ta tana yabawa ƙwarai da juriyar da ta gwada na ɓoye mata ainahin dalilin damuwar ta , cike da rarrashi tace "ma petite soeur mu ma za muyi kewar ki amma kar ki damu kullum za mu dunga yin waya dan Allah kar kisa damuwa a ran kin san ba'a so ki zauna cikin damuwa a halin da kike ciki ko ? "A hankali ta gyaɗa kai tana jin yadda zuciyar ta ke matsewa kamar zata fashe . Murmushi Siyama tayi mata tana ɗan jaan hannun ta tace " to tashi ki zo ki mana rakiya le chauffeur ya zo za mu tai yanzu . Ɗan jimm tayi tana jin wani yanayi marar daɗi na ratsa ta tayi zaton Youssoufa zai sake shigowa suyi wata Sallamar bayan Sallama bayan da Sallamomin da suka dunga yi tun daga jiya har wayewar garin yau da safe kafin ya shirya ya fita daga Sashin nata inda ya kwana . "Maman yumna bari na ɗauko Mayafi na. Tace tana zame hannun ta daga nata ta nufi ɗaya daga cikin ɗakunan ta ' Bayan shigar ta ɗakin bata jima ba ta fito hannun ta riƙe da wata Paper-bag. Bayan ta ƙaraso sai ta miƙawa Siyama ,muryar ta da rauni ta ce "Maman Yumna ga tsaraba ta nan kiyi amfani da kayan ciki. Murmushi Siyama tayi kafin ta sanya hannu ta karɓa tana ɗan leƙen cikin jakar ta ce "ma petite soeur kyauta ce hakka anka min ? Na kouwa gode miki ƙamna ta Allah shi bar ƙauna a tsakani. "Amin . Falmata ta amsa tana Murmushin yaƙe . A bakin mota suka tarar da Biyamuradi Youssouf yana riƙe da hannun Yumna yayi shirin sa tsaf cikin kakin sa na soji da yake matuƙar amsar jikin sa . Tun da Falmata ta samu lafiyar idanun ta yau ce rana ta farko da ta gan shi sanye da kakin soji sai ta shagala wajen kallon sa yadda yayi mata kyau ji take kamar ta ruga da gudu ta rungume shi a ƙarshe kuma ta hana shi tafiya ya zauna a gaban ta tayi ta kallon sa haka tana miƙa godiyar ta ga Ubangiji Youssoufa Namiji ne da kowacce mace zata so ta mallaki irin sa a fagen kyaun suffa da cikar zati irin na cikakken ɗa Namiji yayi zarra . Shi ɗin ma ita ya zubawa ido a tun fitowar su yana nazarin damuwar da take danƙare a fuskar ta wanda a take ya ji tana kassara masa gaɓɓai da a zahiri ma dan haka ne ya ƙi shiga sashin nata yayi mata bankwana saboda yana tsoron abunda ka iya biyo bayan hakan wataƙila ma ya fasa tafiyar . Gyaran muryar da Siyama tayi yasa Falmata tayi saurin ɗauke ganin ta daga kan sa tana yin ɗan baya kaɗan ta riƙo hannun Yumna wacce ta baro Baban ta ta dawo wajen Mamar ta . "Yumna zan yi kewar ki sosai , ta furta hakan tana shafa kan ta . Mayar da ganin ta tayi sashin da Siyama take tsaye "to Maman Yumna Allah ya kiyaye muku hanya dan Allah idan kun isa ki sanar min . "Nima zan yi ƙewar ki ƙamnata Amin nagode sosai dan Allah ki kula muna da kan ki da bébé mu . Gyaɗa kai Falmata tayi tana mayar da ƙwallar da take ji tana cika mata ido taƙi yarda ta sake kallon Sashin da Biyamuradi yake tsaye duk da cewa tana jin idanun sa na yawo a kan ta. chauffeur ya buɗe ƙofar motar Siyama da Yumna suka shiga ganin haka yasa a hankali ta juya tana ɗaga takun ta dan barin wajen. " Fatima . ya ƙira sunan ta . Chak ta tsaya ba tare da ta jiyo ba , ɗan taku yayi ya matso kusa da ƙofar motar cikin amon sa mai ƙarfi yace "je t'aime tellement Et tu me manqueras. Har cikin ran ta ta ji kalmomin sa a hankali ta runtse idanun ta hawayen da suka cika gurbin idon suka gangaro kan ƙuncin ta . Muryar ta na rawa ta furta "Allah ya kiyaye mu ku hanya ya kai ku lafiya Amin . Da sauri kamar ba ita ce ke ɗauke da wannan tirtsetsen cikin ba ta ƙarasa barin wajen idanun ta a rufe da ruwan hawaye . Youssouf da yake tsaye ji yake kamar ya bita ya riƙe ta ya hana ta tafiya amma ya san idan yayi hakan zai ɓata goma ne ɗaya bata gyaru ba . Lokacin da ta ɓacewa ganin sa dan kansa ya shiga motar direba ya jaa suka ɗau hanyar barin-gidan suka kama hanya ɗoɗar zuwa Birnin Tahoua inda yake aiki . Lokacin da Falmata ta koma sashin ta abu na farko da ta fara yi bayan ta ci kuka har ta bawa aku lada ta ji idanun ta sun fara raurawa suna mata alamun ciwo ' Lallaɓawa tayi ta ɗau wayar ta wacce take ji tana ta ɗaukar kiɗa da ko bata duba ba ta san Biyamuradi Youssouf ne ke kira A hankali ta shafa wayar ta kashe tana zunɓuro baki kamar yana ganin ta tace "Na fasa yin Appel vidéo ɗin da kai . **** Duk da cewa tafiyar bata yiwa Siyama armashin da ta so ba amma hakan bai guntule mata jin daɗi da ɗokin ta ba sai hira take yi masa wani ya amsa wani kuwa yayi shiru yana shafe-shafen waya da sarai ta lura da wacce yake faman ƙira Fatima ce . Ko da suka isa jahar Tahoua da gefen Azahar a share a tsaftace suka tarar da gidan dan haka aikin da tayi ba mai yawa bane ba illa kayayyakin su da tayi musu ma'ajiya a muhallin da ya dace ta sake yin wasu 'yan gyararraki da ba'a rasa ba. Kafin ta gama wani Soja da yake hidima da gidan ya zo da cefene dan haka kai tsaye ta shiga kitchen duk da cewa ba sabon ta bane yin girki amma bata gagara iyawa ba dai-dai gwargwado ta zage-damtse dan farantawa Mijin ta tayi girki mai kyau da daɗi Yumna na taya ta da ɓarna . Youssouf kuwa tunda suka zo da aka sauƙe su shi wucewa direba yayi da shi can babban ofishin su inda zasu yi wata ganawa shi da abokan aikin sa . Ba shi ya samu damar komawa gidan ba sai bayan isha'i lokacin da ya shiga gidan tsit babu motsin kome sai na na'urori. bai tarar da Siyama a falon ba sai fa wani daddaɗan ƙamshi da ya shaƙa wanda take ya tado masa da tunanin Fatiman sa domin kuwa ƙamshin irin nata ne a duk inda tayi bigire nan yake jin irin ƙamshin kewar ta mai yawa ya ji tana bin jikin sa , tunda suka taho yake son ya ji lafiyar ta amma taƙi ɗaukar wayar a ƙarshe ma ta kashe ta baki ɗaya kuma tunda ta kashe bata kunna ba . Zama yayi akan kujerar falon yana sunce igiyoyin takalman sa , bai ji tahowar ta ba sai sauƙar kyakkyawan hannun ta da yasha adon ƙunshi ya gani ta ajiye akan hannun sa ta karɓe kunce takalmin da ya fara . Sakar mata yayi yana bin jikin ta da kallo da ta sha ado da wata bugaggiyar shadda Boo ɗinkin bubu tayi ɗaurin ɗankwali mai ban sha'awa jelunan kitson ta da ta haɗa ta tufke ta haɗe cikin ƙaton ribbon ya taimaka wajen ɗago da ɗaurin daga ƙasa sai ya zauna ɗas a kan ta kamar hula . "Siyama ma'abociyar kwalliya ce , daga can ƙasan ran sa ya aiyana haka . Yana kallon ta har ta gama ta ɗago fuskar ta da bata cika fente-fente ba tana masa murmushi ta ce "Bienvenue mon amour et comment va le travail? Sannu. Fuskar sa a sake da taƙaitatcen murmushi yace "ke za'a wa Sannu Maman Yumna da hidmar gida da kaɗaici , ɗakin taro mun ka hige sai yanzou munka kai ga hittowa. bata amsa ba ta miƙe da ɗan murmushi a fuskar ta ta wuce ɗaki daga can ta haɗa masa ruwan wanka . Ya shiga yayi bayan ya gama ya sako ƙananun kaya da basu cika nawi ba a jikin sa ya fito Daga nan abinci ta kawo suka ci tare bayan sun gama ta tattara wajen ta dawo ta zauna daga gefen sa suna kallon TV tare duk da dai ita ba wani jin daɗin kallon take ba saboda tashar labarai ne shi yake ganin kayan sa . Lokacin da ta ga ya ɗau waya sa sai da zuciyar ta ta doka tana satar kallon sa ta ga ya fara ƙira bugu ɗaya biyu , daga can ta ji computer na sanar da shi wayar a kashe take chajin wayar sa ya duba ya ga saura kadan ta mutu dan haka kawai sai ya kashe wayar ya sa a chaji yana jin duk babu daɗi "meyasa Fatima za ta masa wannan horon ? "Biyamuradi Ta ƙira sunan shi Da ido ya amsa mata yana kallon ta . Murmushin yaƙe tayi kafin ta ce "tunda muka zo nayi ta neman wayar ƙamnata a kashe wayar.... Kafin ta ƙarasa Youssouf ya amsa mata fuskar sa na bayyana damuwa "nima itta nake ta ƙira amma ta kar wayar ko mai yassa tayi hakan ? "Watakila batta so ta tsare ma aiki ne , Siyama ta amsa masa tana ɗan nazarin sa ta ɗora da cewa "Amma ko za ka gouda kiran Hajja ne saboda a san halin da ta yini ciki. "Hakka ya kamata, Amma itta telephoné na babu wutta cikin ta. "Bari na ƙira ta da telephoné na sai ta sada  mu da itta Bugu ɗaya Hajja ta ɗau wayar ta tana ɗan gigin bacci tace "hallo waye anan ? Daga can Siyama ta amsa mata tana jin muryar ta ta watsake suka gaisa faran-faran ta ɗora da faɗa mata dalilin ƙiran nan take Hajja ta yunƙura ta fita daga ɗakin ta ta nufi ɗakin Falmata cewa take "kada ma ki katse ƙiran ai yanzu zan kai mata idon ta biyu dan ban jima ba ma da barin ɗakin nata bayan mun gama hira . "Hello Maman Yumna da fatan kun isa lafiya ? daga can Falmata da ta karbi wayar ta furta Shiru ta ji anyi "Hello ta sake cewa. Daga can ɓangaren da tunda ta ɗaga wayar Siyama ta miƙawa Youssoufa "Fatima . Sautin sa ya doki dodon kunnen ta da yasa ta runtse Ido tana jin yadda gangar jikin ta ke sauyawa daga jin amon sa . "Fatima me yassa kin ka kashe min waya unn ? Shiru ta sake yi tana jin sa ya cigaba da cewa "kin sa na shigga damouwa , kar ki sake min ya hakka kin ji kou ? "Fatima "Mon bébé kina ji na ? Sautin kukan ta ya ba shi tabbacin tana jin sa runtse ido yayi yana jin ciwon kukan nata ya fahimci Fatima tana da zafin kishi sosai da sosai da shi a ganin sa ba kome ya kawo hakan ba illa tsananin son da take masa. Ajiyar zuciya yayi daga ƙasan ran sa ya fara harhaɗo kalaman da zai rarrashe zuciyar ta take cike da ƙaunar sa. **** Bayan Awa Ɗaya da Rabi: Rarrashi ya rikiɗe ya koma hira mai cike da raha da ƙaunar juna daga ƙarshe ma suka koma video call kamar ba sa rabu ba kafin daga ƙarshe ya sake wani rarrashin kafin su yi Sallama da alƙawarin gobe za ta gan shi a vidieo call a dai-dai wannan lokacin Zuciyoyin Su cike da nishaɗi da begen juna suka yi Sallama bayan sun aikawa da juna Sumba ta iska . Sai bayan da ya sauƙe wayar ya lura da yadda dare ya shiga wajen shaɗaya da rabi na dare. Yawo yayi da idanun sa a falon sai dai ko alamun wacce yake dubawa bai gani ba , haka kawai ya ji wani irin yanayi na bin jikin sa yana ganin rashin kyautawa kan abunda yayi musamman da ya tuno da cewa da fa wayar ta su ka sha hira shi da Fatima , "anya kana adalci ? Zuciyar sa ta ƙwanƙwashe shi. Cikin rashin kuzari ya miƙe bayan ya kashe kayan kallon ya rufe ko'ina ya nufi ɗakin baccin su ' A hankali ya turo ƙofar cike da son kiyayewa kada ya tada su a baccin da yake hasashen suna tsaka da yin sa . Da shigar sa yayi turus kafin ya ɗan yi duru-duru saboda ido huɗu da suka yi shi da Siyama wacce take zaune daga ƙasa ta tasa laptop a gaba da alama karatu take yi . Murmushin da ta jefe shi da shi lokacin da take zare gilashin idanun ta bai taimaka ba ko kaɗan wajen rage masa yanayin da yake ji a dai-dai lokacin da shi kan sa ya gaza fahimtar ainashin wanne irin yanayi ne ? . "Ya Fatima da Bébé ? Duk suna lahia kou.? "Suna lafiya , ya amsa mata kafin ya zauna daga kan kujera ɗaya tal da take ɗakin yana ɗan sosa ƙeya . "Siyama . Ya ƙira sunan ta yana kallon ta . Cikin nutsuwa ta ɗago kan ta ba tare da ta amsa ba Da taimakon hasken ɗakin ya iya hango yadda launin idanun ta suka sauya su ka yi jaa kaɗan  . "Ba kiyi bacci ba har yanzou ? Ya tambaye ta . Wani irin murmushi mai ciwo tayi tana kawar da kan ta , muryar ta babu ƙarfi sosai ta ce " Ban yi bacci ba Biyamuradi ina jiran ka shiggo muyi Sallama. "Siyama Ya sake ƙiran sunan ta bai jira amsawar ta ba yace . "Duk lokacin da kin ka ji bacci kiyi ko da ina gidan ko bana nan ba sai kin jira mun yi sallama ba...'' "Saboda me ? Ta katse shi da wata irin muryar da take tsakanin harshe da wuyan ta Kallon sa tayi ta ga yadda ya ke duban ta da rauni a cikin idanun sa , kafin ta ɗora da cewa . "Saboda baka sona ? Baka ƙamna ta ? Baka amre ni domin so ba ? Ni matar cushe ce gare ka ? "Siya... Da sauri ta katse shi lokacin da ruwan hawayen ta ke sauƙa yana ɗiga ta cigaba da cewa "Laifi zuciya ta tayi a doumin ta so ka ? Ko kouwa ni nayi laifi da na kassa jumriya akan ƙamnar ka har dai nayi kafiya kan Amren ka ? Da ka ke gwadan rashin ƙamna a fili kake watsi da sha'anin da duk ya shafe ni ? Tasowa yayi ya dawo gaban ta ya zauna yana jin girman laifin sa na masa lulluɓi tunda ya kai girman da har ta kai yau Siyama ta ɗaga Muryar ta . Hannuwan ta da suka ɗau sanyi ya riƙe yana lalubo kalmomin da ya musu ajiya mai nisa da basa taso da kan su sai fa akan wacce aka yi ajiyar su a domin ta yau so yake ya ƙalato su ya yiwa Siyama kyautar su wataƙila sa wanke mata zuciya su samar mata da nutsuwa a cikin hakan babu laifi domin ita ma ta cancanta. "viens chérie yaya ki ke faɗin hakka ? Me yassa za ki ce bani ƙamnar ki ? Bani ƙamnar ki na amre ki har mun ka haihu ? Ina son ki mana Siyama... Zame hannun ta tayi tana girgiza kai lokaci guda tayi wani murmushi mai ciwo muryar ta da 'yar dariyar baƙin-ciki tace . "Kar ka jefe ni da kalmomin aro domin shi kayan aro ai basshi rufe katarar mai su , wannan kalmar ta so ba tawa ce ba ban taɓa samun ta ba ga gurin ka kai tsaye sai ko dan alfarma bani son jin ta domin ba'a halicce ta a zuciyar ka a domin ni ba . Saƙare yayi yana kallon ta wata irin kunyar ta ya ji a lokacin tana tasowa tana danne shi har yana jin kamar bai iya numfashi mai kyau . Ganin yayi shiru ya sa ta miƙewa bayan ta kashe laptop ɗin ta ta tura gefe , wani irin ciwo zuciyar ta ke yi so take ta samu waje tayi kuka yadda ya kamata . Sai dai kafin ta ɗaga ƙafa ta bar gurin ya jawo hannun ta da ƙarfi ta taho gaba ɗaya ta faɗa masa yayi mata kyakkyawar runguma a ƙirjin sa . Kukan da yake cin ta a rai shi ta samu damar yi ta shiga rairawa har jikin ta na tsuma . Biyamuradi Youssoufa ya kasa cewa kome illa rungume ta da yayi tsam yana jin yadda kukan ta ke ratsa jijiyoyin jikin sa suna tsinka masa gudun jini tare da ɗarsa masa wani irin yanayi mai kama da tsoro-tsoro a cikin ran sa "tsoro yake ji na ɗaukar hakkin ta , tsoro yake kar Allah ya kama shi da laifin rashin adalci a tsakanin Matayen sa . Sai da tayi kukan ya ishe ta har ta fara lafawa dan kan ta sannan ya kai hannu a hankali ya riƙo hannun ta ya ɗora shi a saitin ƙirjin sa muryar sa can a ƙasan maƙoshi yace . "Kin ga nan , kin ji yadda zuciyata ke tsanan ta bugu a halin yanzu ? Akan ki ne Siyama tuhuma ta take yi meyasa na ɓata miki Siyama ? Zuciyata na ganin GIRMAN ki ke ABAR GIRMAMAWA kike a gareni , ina jin Kunya idan na ga na ɓata miki Siyama a nan duniya cikin 'ya'ya mata wace ta samu ƙima da girman matsayi kwatankwacin naki a gurina Siyama ? Amsar ita ce babu.' " Yakanar ki ta sayo miki mafi ɗaukakuwar daraja a gurina shin ba za kiyi alfahari da hakan ba ? A hankali ta ɗago kan ta daga cikin ƙirjin sa tana jin yadda ruwan hawayen ta ke ƙafewa zuciyar ta ke tsantsamewa kunnuwan ta ke buɗewa . Kallon da take masa kallo ne na irin " sake faɗa na ji ? Da gaske kake ? Da hannunwan sa biyu ya riƙo fuskar ta yana jin yanayin da yake ji a game da ita na sake ninkuwa har yana neman fin ƙarfin sa so yake kawai ta yarda da abunda yake faɗa mata . "Siyama zuciya ta na girmamaki gangar jikina kuma na buƙatar ki ke ɗaya ce ke da wannan matsayin a guri na da alƙawari na miki watta ba zata samu gurbi ya irin na ki ba , watta ba zata ɗau wannan matsayin ba ki yarda da ni . Ɗan bakin ta da ya faɗaɗa da murmushi yake motsawa da son cewa wani abu shi ya rufe domin a lokacin baya buƙatar tace wani abu . "So , ƙauna , haƙuri , Yakana da kawaicin da ta kwashi shekaru tana gwada masa sun riga sun masa gamsarwar da bai buƙatar ta sake furta kowacce kalma a gare shi a domin wai ta maida masa martanin kalmomin sa lokaci ne yanzu yayi da ita ma zai kyautata mata gwargawdon girman da zuciyar sa ke bata . "Ta gaza tantance a halin da take ciki tsawon lokaci ji take kamar mafarki take za ta farka , kalmar girma ta mata nawi wajen ɗauka kamar yadda zuciyar ta ta gaza wajen jurar irin farin-cikin da take ciki wanda da ɗai a rayuwa bata taɓa samun makamancin sa ba dan haka ta dunga maida masa martanin Soyayyar da yake gwada mata cikin nishaɗi da basu taɓa samun makamancin sa ba a duk zaman auren su . "Shin me ya kai hakan martaba a ce Mijin ka wanda Allah ya umarta da ka girmama shi , da bakin sa yace shi ke girmama ka ? "Ashe ba soyayya ce kaɗai abun nema a wajen Miji ba akwai abunda yafi soyayyar girma da martaba . "Babu shakka daga yau za ta iya tutiya da matsayin da Mijinta ya ɗora ta akai matsayin da bata taɓa tarayya da wata akan sa ba nata ne mallakin ta ita kaɗai . "Ina ma da mata zasu fahimci hakan a duk lokacin da hagu ta ƙi su a gurin Miji suyi amfani da Dama su samarwa da kan su ramin kan su ba tare da sun nace da suyi kafaɗa da kishiya ta fanni ɗaya ba.? Da kuwa gidaje da yawa an zauna lafiya a tsakanin kishiyoyi . Siyama ke ayyana hakan a cikin ran ta bayan bacci ya ɗauke Biyamuradi Youssouf da ita kuma zallar farin cikin da take ciki a yau shi ya hana ta bacci . A karo na biyu ta ɗaga kan ta duk da cewa da duhu a ɗakin so take ta sake ganin hasken fuskar sa ko da sau ɗaya ne kafin bacci ya ɗauke ta . A daren yau son da take masa ya sake ninkuwa ne akan na daa har tana jin kamar ba zata iya ɗauka ba . Cikin bacci ya mayar da kan ta jikin sa ya kwantar tare da sumbatar goshin ta kafin ya cigaba da baccin sa cikin nutsuwa . Ɗan murmushi tayi ta sumbanci ƙirjin sa kafin ta rufe ido baccin da yafi daɗi da kan sa daɗi ya ɗauke ta. **** Abuja Cikin satika ukun da suka biyo bayan barin Sofi Gidan Doctor Hamza wata irin Soyayya mai daɗi da shaƙuwa mai girma ne ya ƙullu tsakanin ma'auratan biyu Doctor Hamza da Yakaka . Musamman da ya kasance daman 'yan uwan juna ne dan haka sai aka yi dace wasu daga cikin halayen su suka zo ɗaya kamar yanayin buƙatuwar halittar su da matsananciyar tsaftar su , yawan ibadar su , da rashin son hayaniyar su dan a wasu lokutan ma shiru gidan yake ɗauka suna gudanar da soyayyar su a aikace ko kaɗan basa gajiya da junan su kusan koyaushe cikin ƙoƙarin farantawa juna suke muddin dai suna tare . A satika ukun har wata 'yar sirantatciyar ƙiba Yakaka tayi ta sake fari tayi fes da ita  , yawan gyaran da take yiwa fatar ta kamar yadda Amnee ta koya mata bayan ta haɗo ta da kayan gyaran yasa kullum jikin ta kamar bayan ƙwai luwai-luwai . Ga ƙamshi na musamman da ya zauna mata saboda turara da take yi gaba ɗayan jikin ta da hakan shi yafi kome sa Doctor Hamza ya liƙe mata kasantuwar sa ma'abocin son kamshi. Ga girki da kullum take yi musu masu gamsarwa da ƙara lafiyar jiki saboda har ajin koyan girki ta shiga a whtsapp na musamman da shahararriyar ƙwararriyar mai koyar da girke-girken nan kuma Marubuciya Maryam Talba ta bude take kuma jagorar azuzuwan musamman domin koyar da mata girke-girke masu gamsar da Maigida, Tare da goyon bayan Doctor Hamza da shi ma yake jin daɗin girkin ta dan haka ya amince ta faɗa ajin Koyan girki Na chef  Maryam Talba (wacce duk take da ra'ayin shiga ajin girkin Chef Maryam Talba duba da cewa Azumi ya gabato Uwargida kina bukatar sabbin darasi kan girke-girke domin gamsar da Maigida da iyalan ki , to kar ki ji kome yi maza ki min direct message insha Allah zan sada ki da Chef din da na san sai kin min godiya a gaba sannan babban abun farin-cikin da za ki tadda shine a kudi mai rahusa za ki fada ajin 👌sai kun zo👍) ***** Yau ta wayi gari cike da burin gwada wani daddaɗan girkin da a jiya Chef Maryam ta gwada musu da yayi matuƙar burge ta . Kamar yadda Chef Maryam ta kware a girke-girken mu na nan gida Nigeria har da na ƙetere ma ba'a bar ta a baya ba ta ƙware a girkin larabawa dan haka yau Yakaka tayi aniyar gwada dafuwar Maqluba wadda dafuwar shinkafa ce da kaza, dankali, ganyayyaki haɗi da sauran sinadaran girki . Maqluba girki ne na mutanan gabas ta tsakiya wanda yake da matuƙar daɗi . Cike da nishaɗi take aikin ta tana yi tana bin ƙira'ar Alkur'ani da ta sa a wayar ta. Kafin ya bayyana ƙamshin sa ya sanar mata da wanzuwar sa a gurin zuwa lokacin da ya shigo kitchen ɗin ta ɗago kan ta a hankali tana jifan sa da wani tsadaddan murmushi . "Habibi barka da tashi , gaskiya ka sha bacci. Ta furta hakan ba tare da ta janye murmushin ta ba Ƙarasowa yayi ya rungume ta ta baya yana ɗora kan sa a kafaɗar ta yace . "Wafaa kin saɓa doka ta meyasa ? Wara ido tayi tana ƙoƙarin juyowa ya hana ta a hankali ta ce "Kayi haƙuri cikin rashin sani ne. "Ba laifi kika yi ba Wafaa , amma ban ji daɗi ba da kika manta cewa na hana ki kiyi aiki ke kaɗai idan har ina gida ko da bacci nake ki dunga tashina muna yi tare . Murmushi mai bayyana haƙora tayi ta ɗan sauƙe ajiyar zuciya lokacin da ta kashe gas saboda girkin ta ya kammala . Tana ƙoƙarin juyowa ya sassauta riƙon da ya mata ta juyo tana fuskantar sa. "Hannun ta ɗaya ta ɗora a ƙirjin sa tana ɗan bubbugawa a shagwaɓe tace "wallahi har hankali na ya tashi ko wani laifin na yi ban sani ba. Dariya yayi yana riƙe hannun ta yace "laifi kika yi mana meyasa za ki wahalar min da ruhina da kika san koyaushe yana nan ne a  tare da ke , meyasa baki tada gangar jikin ba ? Anyi aikin tare da shi ? Murmushi tayi tana kallon sa irin waɗannan kalaman nasa su suka ta dilmiye a cikin ƙaunar sa ba tare da ta ankara ba ko kaɗan baya mata ƙouron kalaman sa na soyayya kamar yadda baya ƙasa a guiwa wajen gwada mata ƙauna a zahiri bai kuma jinkirtawa wajen yaba mata a duk lokacin da tayi wani abun a yaba kome ƙanƙantar sa kuwa ' Maza irin sa sukan sauya akalar zuciyar kowacce mace cikin sauƙi . Sauƙe idanun ta tayi ƙasa tana murmushi saboda wani irin narkakken kallo da yake mata , ita irin salon Soyayyar sa nawi take mata kunya take sa ta har ta dunga jin wani yarrr a jikin ta. Ko kaɗan bata iya masa martanin kalaman sa , kuma bata jin daɗin hakan so take ita ma ta koya su dunga musayar ƙauna kamar abun zai fi armashi . Sautin dariyar sa ta ji da yasa ta ɗago kanta da sauri tana kallon sa sai ta ga idanun sa bayan ta yake kallo . Juya ta yayi yana mata nuni da wasu tattabaru Mata da Miji (aure ) , da suka sauƙa ta gaban tagar kitchen ɗin suna soyayyar su . "Wow look at them Wafaa so lovely. Ya furta hakan muryar sa kasa-kasa yana rungumeta ta baya. Zuba musu ido tayi tana kallon yadda suke sumbatar junan su kamar sa cinye bakin juna, sun matukar birgeta tsuntsaye kenan ma suke wannan soyayyar ? Ba shakka soyayya aba ce mai daɗi. Daga shi har ita shagala suka yi da kallon soyayyar tattabarun mai ban mamaki da Sanya sha'awa tare da nishadi a zuciyar ma'abota soyayya. Basu Ankara ba Matar ta gayyaci Mijin dan Su cimma maƙurar soyayyar Su ganin haka yasa da sauri Yakaka ta ɗaga tafukan ta biyu tana rufe fuskar ta . "Habibi mu bar su hakan nan zasu yi sirrin Su. Ta furta hakan tana ƙoƙarin janye jiki daga wajen . 'Yar dariya Doctor Hamza yayi yana sauƙe mata hannun ta da ta rufe fuskarta da shi Cike da zolaya a muryar sa yace "ki buɗe ido ki kalle su darasi za mu ɗauka mu ma anjima sai mu gwada. tana buɗe idanun ta ta gan su a halin da ita bata so da sauri ta sake rufe ido ta juya tana shigar da kan ta kirjin sa har a cikin ranta kunya ta ji . Rungume ta yayi yana dariya ƙasa-ƙasa kunyar ta na ɗaya daga cikin abunda yasa yake ƙara son ta ,kunya alamun imani ce bayan haka tamkar ado take ga ma'abota ita. Ƙiran wayar sa da aka yi shi ya katse shirun nasu ya sassauta riƙon da yayi mata kafin ya zaro wayar sa daga aljihu.  Cikin ransa cike da addu'ar Allah yasa ba ɗaya daga cikin waɗan da yake zato bane . Addu'ar sa kuwa bata karɓu ba domin kamar yadda ya zata dai Baba Prof ne da kan sa yake ƙiran sa. Cike da ladabi ya ɗaga kiran suka gaisa kafin ya tsinkayi Baa yana masa maganar da yake gujewa tsawon sati guda . "Hamza ka kuwa je kun taho da iyalin taka ? Shiru yayi saboda ya san kawai ya tambaye shi ne ba wai dan bai san cewa bai je ba sai dan ya ba shi damar shigar da uzurin sa. "Ban tafi ba Baa amma yau dai nake son na je Insha Allah . "To ka daure dai ka je saboda kullum sai Mahaifiyar ta ta ƙirani bana son kayi wani abunda zai taɓa mana zumuncin mu na dai faɗa maka ina kuma sake maimaita ma shi aure daman haƙuri ke jagorantar sa sannan ba zaka gina gidan ka ba sai ka zama jajirtatcen Namiji tsayayye sannan gidan ka zai zama yadda ake so . "Ina umartar ka da kaje anjima ka dawo da Matar ka ka kuma cigaba da haƙuri da su su duka biyun aure ibada ne . "To Baa insha Allah zan je Allah ya ƙara girma. "Madallah Allah ya muku Albarka baki ɗaya. "Amin Ya amsa yana sauƙe wayar ya kashe. Ba sai ya faɗa mata ba daga cikin maganganun sa ta fahimci akan me ake zance da lokacin da ta fahimta ba ƙaramar juriya tayi ba wajen ɓoye razanar ta ta juya tana ƙoƙarin zuba musu abincin a farantin da ta ɗauko . "Wafaa ya ƙira sunan . "Na'am ta amsa tana ƙin kallon sa . Ɗan jimm yayi yana juya zancen da yasan dole ya taɓa mata rai kafin ya tattaro juriyar sa yace . "Baa da Amnee sun ce Sofi ta dawo , dan haka anjima zan je mu dawo tare. Wata 'yar fara'ar da take tsakanin laɓɓa ta sakar masa da 'yar dariya tace "Yeehh Anty Sofi Oyo-yo gaskiya naji daɗi Yaya Dacta . Matso ta yayi yana mata rumfa fuskar sa babu walwala yace "me kika ce ? "Cewa nayi naji daɗi . Ta sake faɗin hakan da siririyar murya ganin yadda ya haɗe fuska . "Ba wannan ba da wanne suna na ji kin ƙirani yanzu ? Dariya tayi tana tura shi baya ta ce "Anty zata dawo sunan ka na baya ma zai dawo.. Abincin da ta fara zubawa shi ya hana ya sake riƙe ta amma muryar sa bata ɓoye halin da zuciyar sa take ciki na rashin jin daɗi ba yace "Wafaa kar ki rage ko ɗigo na daga yadda muka saba al'amuran mu dan wai Sofi za ta dawo idan kika yi hakan za mu ɓata ni da ke , umarni ne wannan nake ba ki . Bai sake cewa da ita ƙala ba ya fita daga kitchen. zuciyar ta taji ta ƙuntata "to ita meye laifin ta dan ta ce zata janye sunan da take ƙiran sa da shi a gaban matar sa ? Ita a ganin ta kiyayewa take son yi sanin da tayi Sofi tayi nisa a fagen kishi. Hawayen da suka cika gurbin idanun ta ne suka zubo , wani irin tsoro take ji kan dawowar Sofi ko yaya zaman su zai sake kasancewa ? Jikin ta duk a sanyaye ta gama zuba abincin ta ɗauko ta nufi falon , a kan kujera ta hango shi kafin ta ƙaraso ya taryo ta ya karɓe farantin hannun ta , sai ta koma kitchen ta ɗauko masu kayan sha da ta haɗa . Ɗan shiru ya ratsa tsakani kafin lokacin da ta fara zuba musu haɗaɗɗiyar Maqluba da ƙamshin ta ya ɗau wajen ya tado wa da Doctor Hamza muguwar yunwar da yake ji . "Wow what a delicious ? a complete meal containing, carbs, protein, fats, fibre, essential vitamins and minerals. Da murmushi take kallon sa lokacin da ya kai loma ta farko ya haɗiye ya sake ɗiban wata yana lumshe ido ya cigaba da cewa  . "Wafaa do you know Basmati rice has higher fibre content and is a great option for various meal plans, prevents against Cancer cell formation and prevents constipation against heart health risk.?  Tana ɓoye dariyar ta ta ɗan girgiza masa kai alamun bata sani ba. Kazar da ya ɗauka ya gutsira ita ya nufo bakin ta da sauran . Noƙewa tayi tana dariya tace " ni fa ba kaza zan ci ba kawai shinkafar raina ke so. Wara ido yayi yana mata kallon mamaki kafin yace "Come on ki ci kaza Wafaa chicken is a great source of lean protein and has abundance of selenium, phosphorus, niacin. Haka ba dan ta so ba ta gutsiri kazar ta ci kafin ya cigaba da bata abincin Suna cikin ci tace "Habibi kai baka cin tumatir Sosai ni kuma shi nafi so ka dunga bani sosai. Bayan ya haɗiye abincin bakin sa yace "eh kuma kina da gaskiya domin shi tomato is a great source of vitamin C, potassium, vitamin k1, folate which are great for normal tissue growth and cell function. Dariyar da take ta riƙewa tuntuni ita ce ta kufce mata ta shiga ƙyalƙyalawa har tana kwanciya a jikin kujera , shiru yayi yana kallon ta da murmushi a laɓɓan sa daman burin sa kenan ya ga fara'ar ta farin-cikin sa yana tare da walwalar ta. **** Kamar yadda Doctor Hamza ya alƙawarta A daren ranar bayan Sallar isha'i ya tafi gidan su Sofi domin su dawo tare lokacin da ya ɗora idanun akan ta sai da ya razana saboda ramar da yaga tayi cikin 'yan satika. Yadda yake zaton za ta masa hauka sai ya ga akasin haka sai nan-nan take yi da shi daga ita har Mahaifiyar ta da hakan yasa dole shi ma ya sau jiki suka ɗan taɓa hira da Momy kori kamar kome bai faru ba. Inda ya ɗan ga alamun sauyi daga wurin su bai wuce lokacin da suka kawo masa girke-girken da aka shirya musamman domin shi sannan su ka matsa kan sai ya ci. Shi kuwa ya riga ya ɗebi girkin Yakaka ya ɗora da lafiyayyen kunun aya da ta musu dan haka cikin sa a cike yake ha'in babu masaka tsinke , dan haka ya kafe kan cewa shi babu abunda zai iya sake sanyawa a cikin sa sai kuma gobe. Nan ya ga yadda Sofi tayi kicin-kicin bai bi ta kan ta ba yace tayi sauri ta shirya ta zo su tafi. Ga tunanin sa Momy Kori zata ajiye Sofi a gaban sa ta mata ko da 'yar nasiha ce tunda Baban su baya ƙasar yayi tafiya amma ga mamakin sa ko addu'a Momy Kori bata musu ba . Mamakin sa bai ƙaru ba sai ma lokacin da suka ta shi tafiya yaga Momy Kori ta sa an kinkimi Manyan kulolin abincin nan ta ce wai a kai masu mota su tafi da abincin idan ya so gobe da safe sai Sofi ta ɗumama masa yayi breakfast . Mamakin sa bai ɓuya ba yace "Momy ɗumamen abinci kuma.? Da Allah a mayar da abincin nan a bayar ga masu aiki . Momy Kori za tayi magana Sofi tayi saurin katse ta "eh Momy a mayar da abincin nan Doctor fa baya cin abincin da ya kwana . Wani kallon yatsutsu Momy Kori tayi mata kafin ta kaɗa kai ta ce "to ai shikenan kowa rai ya yiwa daɗi bayan mai shi kai kuma My Son ka bar daɗi tunda baka cin ɗumame sannu ka ji baƙin bature . Daga haka tayi juyawar ta cikin gida su kuma suka shige mota . A hanyar su ta komawa gida Sofi sai shisshige masa take tare da bayyana masa zallar ƙewar sa da tayi . A can-can yake amsa mata saboda ba wai ya huce bane gaba ɗaya. Bai ankara ba ya ji ta faɗo mai jiki gaba ɗaya ƙiris ya rage kan motar ta kufce masa yayi saurin gangarawa gefen titi. Ransa a matuƙar ɓace ya waiga yana kallon ta "Sofi wanne irin shirme ne wannan ki... Bata ba bar shi ya ƙarasa abunda yake son cewa ba sakamakon haɗe fuskar ta da tayi da ta shi. Sun ɗau lokaci a haka kafin ya zame fuskar sa bai ce ma ta kome ba ya fara ƙoƙarin tada motar yana dai-daita nutsuwar sa ' Ba sabon abu bane a wajen sa Sofi ta  nema shi da kan ta amma yau sai ya ji sam bata wani burge shi ba kamar baya , har ji yayi tana ɗan ba shi haushi-haushi , ya fara sabo da yadda ake ɗan jaa masa aji yana nema ana ɗan nan-noƙewa ana zille masa hakan yana ba shi nishaɗi tare da sa shi ya ji cewa lalle fa shi Namiji ne . "Sofi ki bari nayi driving please kar ki sake taɓa ni. Bata amsa masa ba illa wani shaiɗanin murmushi da take jifan sa da shi tana wani kashe masa ido ɗaya . Lokacin da suka ƙarasa gida Sofi ta riga Doctor Hamza sauƙa a motar dan haka ita ta riga shi takawa zuwa wajen ƙofar kai tsaye ta miƙa hannu ta ƙwanƙwasa ƙofar da ƙarfi Yakaka wacce take zaune zaman jiran su zuciyar ta ta doka da ƙarfi dan sanin bugun ƙofar ko na waye . A hankali ta miƙe ta ƙarasa gaban ƙofar kafin ta buɗe sai da tayi addu'a sannan ta miƙa hannu a hankali ta buɗe ƙofar  . Kallon-kallo aka yi a tsakanin su kafin Yakaka ta ƙalato murmushi ta ɗora akan fuskar ta dai-dai da ƙarasowar Doctor Hamza ta ce "Anty Sofi sannu da zuwa . Sofi wacce fuskar take ɓoye yanayin halin da zuciyar ta take ciki ta miƙa hannunwan ta duk biyu ta rungumo Yakaka. "I miss you so much Lil how are you? Ta furta hakan kafin kuma ta sake ta  tana mai tura ta baya ta samarwa da kan ta hanyar shiga gidan ta wuce kai tsaye ba tare da ta sake kallon Yakaka ba. Yakaka bata dawo nutsuwar ta ba sai da ta ji sanyin hannun Doctor Hamza ya riƙe nata hannuwan "Wafaa mu shiga ciki . Cikin wani irin yanayi Sofi take bin gidan da kallo kamar an sauya mata shi ta ko'ina ƙamshi ne ke ta shi shiru falon sai ƙira'ar kur'ani da ke fitowa ta sifuku . Akan kujerar da ta saba zama nan ta zauna tana harɗe ƙafafu ta miƙa hannu ta ɗau Remote tana ƙoƙarin sauya tasha . A ɗarare Yakaka ta zauna a kujerar da take kusa da ƙofa shi kuma Doctor Hamza kai tsaye ya wuce ɗakin sa . "Anty Sofi ina wuni.? Ya Su Momy ? Yakaka ta furta hakan tana kallon Sofi . Wani irin ɗago kai Sofi tayi ta tsattsare ta da ido tsawon daƙiƙai fiye da hamsin irin kallon da take mata ya kaɗa mata ciki har yasa ta nemi diriricewa . Wani mummunan tsaki Sofi ta jaa da Yakaka ta ji shi har tsakiyar kan ta . Lokaci ɗaya ta ɗauke kan ta a fusace tana kaɗa kai. Nan take ta tunanin kama kan ta ya faɗo mata dan haka bata sake cewa ƙala ba sai ta ɗau wayar ta . Zaman shirun da yake cike da ƙosawa daga ɓangaren su duk biyun ne ya miƙa suna jiran fitowar Doctor Hamza wanda sai da ya shafe fiye da mintoci talatin dan kuwa bayan wanka da yayi sai da yayi sallolin sa na shaf'i da watir . Sannan ya fito falon ya same su kamar wasu gumaka , ita Yakaka kan ta yana ƙasa tana amfani da wayar ta ita kuwa Sofi sai sauya tasha take , bayan ya musu Sallama bai ɗau lokaci ba ya musu 'yar gajeruwar nasiha da ƙare ta da gargaɗi tare da hannuka mai-sanda ga Sofi kan cewa babu shakka shi ba zai sake ɗaukar raini ko rashin kunya tare da neman fitina ba dole ne kowaccen su ta zauna da 'yar uwar ta lafiya a ƙarshe ya sake musu batun rabon kwana inda ya tabbatar da yin ƙwana ɗai-ɗaya a matsayin ranakun girkin kowaccen su ' Bayan gama nasihar sa da dukkanin su suka nuna Amincewar su tare da ɗaukar gargaɗin sa ita Yakaka miƙewa tayi bayan ta musu Sallama. Taku ɗaya tayi shi ma Doctor Hamza ya miƙe , yana yin taku ɗaya ya riƙo hannun ta da yazo dai-dai da jin sauƙar hannun Sofi da yayi a cikin ɗaya hannun nasa. Yakaka tana juyowa idanun ta suka sauƙa akan hannun sa da Sofi ta riƙe wani abu ta ji ya soki zuciyar ta da yasa da sauri ta zame hannun ta daga cikin na shi . Ba tare da ta sake juyowa ba ta nufi ɗaki tana shiga ta murɗa ɗan makulli ta rufe . Jikin ta kamar babu lakka ta samu wajen zama a bakin gado . Bata ankara ba kuka ya taho mata ta kai hannun ta biyu ta toshe bakin ta . Ta kasa sanin dalilin da yasa zuciyar ta ke ƙonewa bayan kuma ba yau ne ba rana ta farko da Sofi ta fara riƙe Doctor Hamza a gaban ta amma a baya bata taɓa jin irin yadda take ji yanzu ba ko me yasa ? Kukan ta chak ya tsaya lokacin da ta ji ya taɓa ƙofar cikin kwantatciyar muryar sa yake ƙiran sunan ta . Shiru tayi ba tare da ta amsa ba "Yau lokacin Sofiya ne Yakaka kar ki aikata abunda idan aka aikata miki ba za ki so ba. Zuciyar ta ta mata gargaɗi mai kama da tunasarwa , dan haka taƙi yarda tayi ko da ƙwaƙƙwaran motsi haka tana jin sa ya ɗan yi mintoci biyu zuwa uku yana taɓa ƙofar kafin ta ji takun sa yana barin wajen . Silalewa tayi ta kwanta ruwan hawayen idanun ta na hagu na shiga cikin na dama . **** Washegari da safe lokacin da Doctor Hamza ya sauƙo daga ɗakin Sofi a kitchen ya tarar da ita tana aikin ta hankali kwance  duk yadda ya so ya hango wani sauyi a tare da ita bai ga ko alama ba daga yadda take masa bata sauya ba . Sai ya ji ta saƙe ƙima a idanun sa ƙaunar ta kuma ta sake ninkuwa a zuciyar sa babu shakka managarciya ce tana kuma da dattaku. Shi ya taya ta suka ƙarasa aikin kafin a gurguje ya shirya kafin ya gama shiri ta haɗa musu abin karyawa . Yana gaf da kammala Breakfast Sofi ta sauƙo yau dai da alama ta ji faɗan Doctor domin doguwar riga ce a jikin ta mai faɗi wacce bata ƙarasa ƙasa ba ta tsaya gaba kadan da guiwar ta sai hula da ta sa ta rufe kan ta . Kadaran-kadahan ta amsa gaisuwar Yakaka kafin tace mata "zuba min abincin na ga ko zan iya ci . Da sauri Yakaka ta ɗau faranti ta zuba mata abincin butter chicken ne tare da khubsa. Tun Sofi tana ci tana wani gatsine-gatsine har dai ta sau jiki daɗin girki ya kwashe ta ta buɗe baki tana wurga loma bayan loma . "Doctor wannan Butter Chicken ɗin kamar daga HH Continental aka yi order ko? Dan naji irin dandanon girkin su ne.  Ta gefen ido ya dube ta dai-dai lokacin da yake miƙewa ya ce "Ni da nake da Mata kamar Wafaa yaushe zan tafi yawon gidan sayar da abinci ai wannan ya zama tarihi sofiya . Hannun Yakaka ya kama "Wafaa mu je ki min rakiya ni zan tafi . Sofi tana son miƙewa amma daɗin abinci ya danne ta dole tana ji tana gani Yakaka ta tafi raka Doctor Hamza ita tana kai lomar girkin Yakaka. Bayan ta dawo daga rakiyar sa ta tarar Sofi ta gama cin abincin ta bar kome a wajen ta koma kan kujera ta hakimce . Bata gaji ba ta tattara kwanukan ta kai kitchen ta wanke . A ɗarare ta dawo falon ta zauna akwai wani series ne da take son kallo da bata samu damar gani ba jiya ta san suna maimaitawa da safe . Tana zama ta ji Sofi ta jaa wani ƙaton tsaki. A hankali ta miƙa ɗaga idanun tana kallon ta irin mummunan kallon jiya shi ta hango a idanun Sofi . Har ga Allah tsoron yanayin kallon take domin kallo ne irin na hatsabiban mutane mugaye , kallo ne da yake ɗauke da saƙonni  masu zafi tare da ƙaƙƙarfan gargaɗi . Ciɗak¡ ta miƙe bata tsaya ba sai ta wuce ɗaki tana jin lokacin da Sofi tayi wata ƙwafa mai ƙarfi . Tana shiga wayar ta ta ɗauka ta ƙira Amnee suka gaisa wacce ta dunga mata nasiha tana kwantar mata da hankali kan dawowar Sofi a ƙarshe ta miƙawa Mamar su wayar . Suka gaisa kafin su yi 'yar hira da rabin ta labarin diramar Bulama ne wanda aka kai shi makarantar kwana ta firamari amma ya gudo da kukan sa da kome a cewar sa ba zai iya barin Mamar Bulama ba . Yakaka ta yi ta dariya tana jin ƙauna tare da tausayin ƙanin ta wanda ba su wani shaƙu da juna ba. A ƙarshe suka yi Sallama tana sauƙe wayar ta ƙira Falmata nan ma hirar suka sha sai dai a cikin muryar Falmatan ta iya jin tana da damuwa da nan take hankalin ta ya tashi dan haka ta matsa mata kan sai faɗa mata me yake damun ta ? Ko haihuwar ce ta zo ? Falmata bata ɓoyewa Yakaka kome nan ta faɗa mata irin matsananciyar damuwar da take ciki kan barin ta da Youssouf yayi ya tafi wajen aiki ta ɗora da cewa "kuma fa Yakaka sau uku kawai muke waya a rana kuma sau biyu kawai muke Appel vidéo a rana kafin ya tafi kuma ba haka ya min alƙawari ba cewa yayi kawai koyaushe yana tare da ni . Shiru Yakaka tayi tana jinjina rikicin Falmata a zuciyar ta kafin ta ce "Falmata waya har sau uku a rana ? Ga kuma vidieo call ? Sau biyar fa kenan kike jin sa bai yi yawa ba Falmata ? Kin san fa tare da matar sa yake a can , sannan ita ma tana da hakki a kan sa bakya ganin za ki shiga hakkin ta dayawa idan ya zama koyaushe kuna tare a waya ? Ni dai fatana Allah yasa bakwa doguwar wayar dare Falmata abunda duk ba za ka so ayi ma ba kar fa ka yiwa wanin ka ' Tsit Falmata tayi daga can tana ɗan turo baki kamar Yakaka na ganin ta sai cewa tayi "to ai nima ina da hakkin ni ba barina yayi ba ma gaba ɗaya ya tafi da ita ba ? ina cewa kullum tare suke kwana ? Meye dan kawai mun yi waya ? Yakaka tana danne dariyar ta ta ce "a ah wallahi da kome muddin aka ce za ki dunga ratsa tsakanin lokutan da ya kamata ace yana tare da ita to ba shakka kina shiga hakkin ta haba mana Falmata ban fa san ki da zalunci ba , dan Miji yafi son ki kar ki yadda ki biye masa ya dunga ƙuntatawa matar sa . Ni yanzu da Yaya dakta yafi son Sofi akaina za ki so ya dunga min abunda babu daɗi akan ta ? Girgiza kai Falmata tayi tana jin duk jikinta yayi sanyi ta ce "ki daina cewa haka Yakaka Yaya dakta yana son ki ba zai taɓa walakanta ki akan Sofi ba. "Kuma nima ba wai so nake ya dunga walakanta matar sa akaina ba kawai dai. Ɗan shiru tayi tana numfasawa kafin ta ce "Yakaka ina son shi ne dayawa zuciyata tana min ciwo idan har na tuno yana can tare da ita ni kuma ga ni nan da ciki himm ina fama. "Ki rage kishi Falmata kowacce mace tana son Mijinta amma domin a zauna lafiya babu cutarwa sai a dunga sassautawa ana tausar zuciya kin jin ko Gimbiya Falmata., ke ce fa Uwargidan Sarki watarana uwayen gida da kawaici aka san su domin suke jagorar Gida . Sassauƙar dariya Falmata tayi tana jin ranta na yin sanyi ƙaunar 'yar uwar ta na kawo mata **** Kafin cikar sati ƙarfi da yaji Yakaka ta koma zaman ɗaki saboda yadda Sofi ta kasa ta tsare alhalin ta san Yakaka tana matuƙar shakkun ta . Muddin ta fito falo to aiki za tayi ta bar wajen ko kuma idan Doctor Hamza yana nan wanda shi bai san yadda yinin su yake kasancewa ba idan baya gidan . Babu abinda yafi daɗa tayarwa da Yakaka hankali irin ji da tayi Doctor Hamza a jiya da dare yace cikin kwanaki biyu masu zuwa zai yi tafiya zuwa jahar Kano za shi asibitin koyarwa na Kano yin wani aiki na kwanaki uku "kenan zai bar su daga ita sai Sofi a gidan 'yar sakewar ma da take samu tayi a cikin awowi ishirin da huɗun idan yana nan zasu zama babu . Hakan ya daɗa sanyayar mata da jiki har wani ɗan zazaaɓi take ji yana kama ta bayan bugun zuciyar ta da take ji yana sauyawa a bayan kowacce sa'a ɗaya ga kasala da ta dirar mata . Bayan fitar sa aiki da ƙyar ta iya lallaɓawa ta fito yin girkin rana da ta san Sofi za ta iya buƙata ba wai dan cikin ta ba saboda ita gaba ɗaya ma yau tunda ta tashi bata sha'awar kome dan ko da suka zauna karin kumallo bata iya cin kome ba sai ruwan shai da ta zubawa cikin ta. Ba irin rarrashin da Doctor Hamza bai mata ba kan ta ci abinci amma ta gagara dan kan shi yayi shiru ya bar ta bayan ya gama nazarin ta. Fitowar ta daga ɗakin ya zo lokaci guda da ƙwanƙwasa ƙofar gidan da aka yi dan haka ta ɗan saurara jin ana sake ƙwanƙwasawa yasa ta taho ta buɗe ƙofar . Musayar kallo suka yi ita da wacce take  tsaye a dokin ƙofar tana jifan ta da siririn murmushi mai tarin ma'anoni . An-anty Samy . Ta ambata a harɗe , "Yaks Amarya a gidan Doctor , matsa min hanya mana na wuce ko kuwa na koma ne ba'a maraba da ni ? Da sauri ta matsa tana girgiza kai da 'yar fara'a tace "a ah ina maraba da ke mana Anty Samy sannu da zuwa . Tayi gaba Samy baby ta bi bayan ta tana ƙare mata kallo . Suna ƙarasawa tsakiyar Falon Sofi na sauƙowa daga sama wata 'yar shewa suka yi ita da Samy Baby kafin su taho su rungume juna suna 'yan ƙananun maganganun su na shaiɗana . Samy baby za ta zauna Sofi tayi maza ta hana ta "friend me za ki zauna yi anan ? Ta shi mu tafi sama akwai muhimman maganganun da kin san nan ba muhallin yin su bane ba . "Ok friend Samy baby ta furta haka tana miƙewa tsaye ta ɗau jakar ta kafin ta mayar da ganin ta kan Yakaka wacce take rakuɓe a gefe wata 'yar iskar dariya tayi mai kama da shewa "Hehehe Yaks kenan ka ga manyan amare masu harin miƙamin uwargida an gaishe ki  Yaks da tsaurin ido . Shiru Yakaka tayi bata ce ƙala ba gaisuwar da ta yi niyyar yi ma ta fasa jin yadda Samy Baby take mata ba'a sarai ta fahimta . Kitchen ta koma su kuma su ka hau sama suna shiga ɗaki Samy Baby ta lailayo wata ashariya ta kwatsawa Sofi . "Kina me Sofi ? Nace kina me har kika bari yarinyar nan ta samu sakewar da zata fara haramar ajiye ƙwai a gidan nan ? Na shiga uku Sofi ina mai tabbatar miki taki ta kusan ƙarewa a gidan nan ..... Sofi da lokaci ɗaya ta diririce idanun ta suka sake shigewa ciki da in'ina a muryar ta tace "me..me ..kika ce ban..ban fahimta ba wanne irin ƙwai kuma kamar wata kaza' "Yo ai ga ki nan babbar kaza Sofi tunda har kika kasa gane Yarinyar nan Yaks tana da shigar ciki kike zaune baki sake baki ɗau kowanne irin mataki ba... Bata ankara ba ta ji Sofi ta sakar mata Mari da yasa shiru ya gifta wajen . Kafin ta tsinkayo muryar Sofi tana cewa "kar ki sake min wannan mummunan Fatan mummunan zancen , "kin yi hauka ne Sofi za ki mare ni ? "A turu nake Samira ya za ki zo kina barazanar fasa min zuciya da mugun fata ki sa na faɗi na mutu tun kwanana bai ƙare ba . Gyara fuska Samy Baby tana ƙoƙarin shanye fushin ta saboda tarkon da take son ɗanawa kar ya lalace ta sassauta muryar tace "Wallahi tallahi I swear Sofi Yarinyar nan ciki ne da ita ki nutsu ki dawo hankalin ki tun wuri mu yiwa tufka hanci kafi.... Wani razanannan ihu da Sofi tayi da ya amsa gidan gaba ɗaya sai da yasa Yakaka wacce take kitchen ta zabura tana dafe ƙirji a take taji zuciyar ta ta hautsina da daman tunda tafara girkin warin Albasa ke ɗaga mata hankali. Ba shiri ta bar baro kitchen ta wuce ɗaki tana mayar da numfashi "anya Sofi kan ta ɗaya ? "Samira da gaske kike ? da gaske kike da gaske ? Kamar an safure ta ta miƙe tayi hanyar fita daga ɗakin da gudu Samy baby ta bita ta riƙo ta . Kufcewa tayi tana watsa mata wani mugun kallo kafin cikin muryar da ta buɗu kamar ba ta ta ba tace "ki bar ni naje na kashe ta na farka mata ciki na zo miki da ɗan tayin cikin na ta wallahi sai na kashe ta. Kallon baki da hankali Samy baby ta jefa mata kafin ta ce . "Dallah Sofi ki nutsu ya kike abu kamar wacce ba tayi karatu ba ? Kina abu kamar wata jahila kina tunanin yanzu idan kika je kika kashe 'yar mutane ke ma za ki rayu da Hamzan ne ba tare da an miki ɗaurin rai da rai ba ko kuwa ke ma a kashe ki. "Na yarda a kashe ni idan na kashe ta akan dai mu rayu ni da ita alhalin ta raba ni da farin-ciki na ina ji ina gani bakin-ciki zai kashe ni na mutu na bar mata duniyar su rayu ita da Mijina . "Na yarda za ta mutu amma ba ta irin wannan hanyar da kike son bi ba ko da kashe ta kike son yi ki bari sai an kauda-bara ta yadda za ki kashe ba tare da an samu mai iya ɗaga ido ya dube ki ba ko kuwa ma kawai a mata abunda zai kashe ta ba tare da an zarge ki ba . "Ta yaya faɗa min hanyar ? Sofi ta furta hakan jikin ta har wani mazari yake , a kaikaice Samy baby ta dube ta cikin ran ta kuwa dariya take kwasa "Yau Sofi uwar bin Bokaye har wata nahiyar ita ke tambayar ta yaya za'a yi ? Lalle notikan cikin kan Sofi sun kwance baki ɗaya . Gyara zama tayi tana jin Allah ne ya kawo mata hanyar warwarewar tata matsalar da kome ya kwaɓe mata bariki tana ƙoƙarin kwashe kayan ta daga kanta ta juya mata baya ta bar ta a cikin rana dan kuwa ko Alhaji Gali a halin yanzu fiye da watanni uku kenan ta daina ganin ƙeyar sa alhalin lokacin biyan kuɗin gidan haya yayi haka tana ji tana gani bayan ƙara mata sati biyu da masu gidan suka yi suka zo a ƙarshe suka kore ta sai gidan ɗaya daga cikin abokan shaiɗanan ta ta koma da ko kaɗan ba jin daɗin zaman gidan take ba saboda ba shi da wani hali sosai irin mazan nan ne da Zina ta aure su wanda ko basu da sisi sai sun yi ta. Fahimtar hakan da tayi yasa ta fara ƙulla wacce za ta fissheta idan zaman Abujan ya gagara ne tana iya komawa ko Damaturi ne ta karkaɗe kwalin ta ta shiga neman aikin da za tayi ta riƙe kan ta dan kuwa ko a mafarki ta san bata doshi Maiduguri gidan Ubanta ba bata ma da matsugunni a gidan sannan ita a karan kanta bata jin za ta iya rayuwa ƙarƙashin iyayen ta. Sai dai me ? Kuɗaɗen da suke account  ɗin ta ba zasu ishe ta yin irin rayuwar jin daɗin da take tsarawa kan ta ba ko da ta koma Damaturu domin so take ta shiga gari sosai ta wataya a ƙarshe ta samu wani ɗan Matashin kyakkyawan Saurayi haka ta chaka masa su yi aure . Dan haka ido rufe take neman kuɗi tunda kuwa yanzu dama ta samu da zata iya samun su daga Sofi to me za ta jira ? Muryar Sofi ta katse mata tunani ta da take cewa " Ni kin hana ni naje na aiwatar da manufata ke kuma kin yi zaune shiru baki kawo wata hanyar ba ki faɗa min ya zan yi ?. "Sofi ki buɗe bakin Aljihu kiyi ɓarin kuɗin na san dai kin Fahimceni ni kuma na miki alƙawarin ko nan da birnin Sin ne zan je miki wurin Boka ba sai kin ma tafi da kan ki ba bare har a iya zargin ki . Da wata irin Murya Sofi ta ce " ki koma min karnataka Samira gurin Bokan da ya min aiki akan zuciyar Doctor zan baki adireshin sa da kome sannan zan bayar da kuɗin da zai ishe ki har kije ki dawo da kuma kuɗin aikin sa , bana so na motsa ma daga tsakanin su domin ko kallo bana so ya sake shiga tsakanin su .... Samy Baby wacce tafi zaƙuwa da zancen kuɗin jin tarkon ta yayi kamuwa tace "amma fa kin san kuɗaɗen dayawa Friend.. "Ko miliyan ishirin ne zan sayar da gwalagwalai na na baki kuɗin bana so a ɗau lokaci nasan kin san manyan mutane a ƙasan nan dan haka samun visa ba zai miki wahala ba idan son samu ne cikin satin nan ki tafi kai ni idan zai yiwu ma cikin kwanaki biyu masu zuwa saboda bana so bana kuma fatan yarinyar nan da ita da abunda ke cikin ta su sake yin sati ɗaya a duniya . Nisawa tayi tana gatsa gefen bakin ta da haƙori tace " Sannan so nake na kashe ta da hannun na Samira da hannu na nake son kashe ta shine kaɗai abunda zan iya mata da zai sa zuciyata ta wanku daga baƙin-cikin da ta samu a ta sanadin ta dan haka daga kin isa can an yi aikin kawai ki ƙirani ki sanar min ina mai tabbatar miki da sai dai ki dawo ki tarar ana zaman makokin mutuwar ta . Shiru Samy Baby tayi tana kallon Sofi cikin ran ta tana girmama rashin Imani irin na Sofi yau ta zama rana ta farko da ta fara jin shakkun samuwar cikakken hankali ga Sofi to kodai tana da rauhanai ne ????? Ko kuwa Mai rabon shan duka ne da baya jin Bari Assalam Alaikum masu karatu. Albishirin ku ? Na san kun ce goro goriya goro . Yau Maman 'yan biyu tagwayen shafuka ta muku. Ina nufin kar ku motsa shafin nan tare yake da ɗan uwan sa da yakasance kuma murfi na baki ɗayan littafin Mafari insha Allah . A sha karatu lafiya . [4/15, 8:17 PM] +234 706 503 6187: MAFARI            ( HARGITSIN RAYUWA) UMM'MUAZ KARSHE (A) A daren ranar Doctor Hamza bai dawo daga aiki ya tarar da Sofi a gida ba saboda tunda rana suka fice ita da Samy ko Yakaka bata san fitar su ba . Hakan ba ƙaramin ɓatawa Doctor Hamza rai ya yi ba saboda ai tsagoron raini ne matar auren ka ta fita unguwa ta kai har dare ba tare da ta nemi iznin ka ba . Sai dai halin rashin lafiyan da ya zo ya tarar da Yakaka a ciki ya ɗauke masa hankali daga kula haukar Sofi . Nan take ya shiga bata duk wata kulawar da ta dace domin samun tabbacin abinda yake zato . Maƙurar farin-cikin da zai iya cewa bai taɓa jin yanayin sa ba ya tabbata a zuciya da kewayen jinin jikin sa baki ɗaya lokacin da gwajin fitsarin da ya yiwa Yakaka ya bayyana masa da tabbatuwar zaton sa Yakaka tana ɗauke da gudan jinin sa a Mahaifar ta nan da wasu watanni zai zama uba bayan shekaru bakwai da ya kwashe da yin auren sa na farko wanda hakan ya sadar da shi cikar shekarun sa arba'in cif ba tare da ya samu ɗan kan sa ba . Sai fa yanzu da Allah yayi tsiron halittar gudan jinin sa a tare da Yakaka shi kuwa da wacce irin kalma zai miƙawa Ubangiji godiyar sa ? Ganin sa ya mayar kan Yakaka wacce take bacci hankalin ta kwance da ba domin larurar saurin bacci na mata masu ƙaramin ciki ba a ɗan zaman su da yanzu-yanzu tayi fitsari ta ba shi yayi awu bai ci ace kafin ya gama gwajin har tayi bacci ba . Fuskar ta ya tsirawa idanu yana jin wani ƙaunar ta mai ƙarfi tana sake fisgar sa har yana jin kamar babu wani sarari da yayi saura a zuciyar sa da ƙaunar ta bata riga ta cika ba . A hankali ya ɗaga hannu yana shafar kumatun ta da suka sake yin suɓulɓul suna ƙyalli na musamman . Zazzaɓin da ya dawo ya tarar da shi ya rufe ta sosai a yanzu ya sauƙa saboda ya bata maganin sauƙe zafin jiki ta sha . "Wafaa . Ya ƙira sunan ta a hankali yana ɗan hura mata iska a fuskar ta ' Buɗe idanun ta da suka yi nawi tayi tana kallon sa a raunace . "Wafaa yaya kike jin jikin yanzu ? Za ki iya tashi muyi sallah ? "Habibi nayi sallar isha ina jin bacci sosai ni. "Na san kin yi wannan Sallar miƙa godiyar mu ga Ubangiji za muyi da yayi mana kyautar sa mafi girma . Hannun sa ya kai ya ɗora akan cikin ta kafin cikin taushin murya yana kallon idanun ta ya cigaba da cewa "Allah ya arzuta mu da samun rabo , Wafaa we are going to have a baby, zan zama Baba Wafaa za ki Haifa min Baby . "Da gaske ? tace da shi tana ƙoƙarin miƙewa zaune ya taimaka mata ta zauna.' Yana murmushi ya amsa mata "Da gaske Wafaa na baki Baby i am gonna be a Daddy. Wani irin yanayi ta ji mai sanyi tundaga ƙasan ran ta da ya chakuɗu da kunyar ta ta halitta dan haka ta tafi da sauri ta shige jikin sa tana ɓoye fuskar ta a ƙirjin sa . Dariyar da bata da sauti yayi yana riƙe da ita ya miƙe kafin ya sake cewa " Alhamdulillah for blessing us in the most special way as a Mum and Dad. Ya ɗago ta a hankali ya sumbanci goshin ta sannan ya sake cewa "muyi Sallah Wafaa domin mu nunawa Ubangiji godiyar mu. Gyaɗa kai tayi ba tare da ta amsa ba . Tsananin farin-cikin da yake ciki a daren ya mantar da shi takaicin Sofi dan ko da ta dawo tana wani kame-kamen ta lokacin da ta shigo falon ta tarar da shi yana aikin sa a laptop Yakaka kuma tana bacci a jikin sa . Wajen ƙarfe goma saura na dare za ta fara masa ƙwarƙwasa ya ɗora hannun sa akan laɓɓan sa yace "shittt please Sofi kar kiyi hayaniya ki tayar da ita a bacci tana buƙatar hutu Sosai bana son abinda zai dame ta . Wani sakototo Sofi tayi baki sake tana kallon sa . "yau ga sabon salo kuma , kullum abun daɗa lalacewa yake , ta aiyana hakan daga cikin ran ta . kafin ta mayar da ganin ta kan Yakaka wacce ta juya baya tana kwance akan kujera tayi matashin kai da cinyar sa fuskar ta na fuskantar jikin sa' Hayaƙi-hayaƙi ta ji yana safko mata yana sanya ta gani dusu-dusu . "Bata da lafiya ne ? Ta furta hakan a shaƙe tana tattaro duk wata sauran juriya da ta rage mata . Murmushi Doctor Hamza yayi da har take Iya hango ƙyallin haƙoran sa da muryar sa mai cike da nutsuwar da bata ɓoye halin farin-cikin da yake ciki ba yace "Sofi we are pregnant insha Allah in nine months we will welcome a new bundle of joy into our family. Kamar wacce aka dokawa guduma a ka haka Sofi ta ji, kunnuwan ta suka rabu da ji na ɗan wani lokaci duk kuwa da cewa a ɗazu Samira ta faɗa mata batun cikin Yakaka amma bata ji dukan zancen irin yanzu ba dan kuwa a ɗazu tana da ƙarfin jikin iya yin zabure-zabure a yanzu kuwa da  zancen ya tabbata cewa dai Doctor Hamzan tane ya yiwa Yakaka ciki ji tayi duk wata jijiyar jikin ta tayi tsayuwa daga barin yin aiki na wucin gadi . A yau taurin zuciyar ta gaza yin tasiri yayi domin kuwa ruwan hawaye ne ya ɓalle mata kamar an buɗa famfo . Sai shiƙar kukan ta Doctor Hamza ya ji wanda ya mayar da kan sa ga aikin sa . Tsam yayi yana jin ɗan guntun tausayin ta na kawo masa , daga can ƙasan ran sa sai ya ji kamar fa bai kyauta ba yadda ya sanar mata da batun cikin Yakaka dole za ta iya jin babu daɗi tunda ita Allah bai bata ba musamman da yakasance Sofi tana da bala'in kishi. A hankali ya ɗago kan sa yana kallon ta sai dai kafin yayi wani yunƙuri ta miƙe kamar ana tunkuɗa ta ta bar wajen . Girgiza kai yayi yana mai mayar da kan sa ga aikin sa da yake so ya kammala kafin gobe saboda a gobe da yamma yake so ya bar garin zuwa Kano . Washegari D octor Hamza da kansa ya shiga kitchen domin samarwa Yakaka da abunda za ta ci saboda kusan kwana tayi da zazzaɓi asubar farko kuma ta fara Amai . Dan haka ya kama ta zuwa falo ya kunna mata tv yace tayi kallo kafin ya gama haɗa mata abun karyawa. Ba dan ta so ba ta haƙura ta bar shi ya shiga kitchen sai dan ko kaɗan bata jin ƙarfin jikin ta wata irin kasala ce take bin gaɓɓan jikin ta jikin ta babu ƙarfi gefe guda kuma bata son warin Albasa da tasan muddin ta shiga kitchen to kuwa sai ta shaƙa . Lokacin da ya gama ya kawo mata bata wani ci dankalin da ya kawo mata tare da ƙwai na kirki ba tace ta ƙoshi . Yana tsakiya da rarrashin ta kan ta daure ta sake ci kaɗan Sofi ta sauƙo bata dubi inda suke ba ta zauna akan kujera ta ɗau remote. Lokacin da ya dubi fuskar ta sai da zuciyar sa ta doka da karfi ganin yadda fuskar tata ta kumbura suntum idanun ta kuwa har kamar kwanciyar jini. Da sauri ya baro Yakaka ya juyo gare ta "Subhananlah Sofi me ya same ki haka ? cikin dare ɓarayi sun shigo gidannan ne ? Ba tare da ta dube shi ba tace "Da aljanu muka yi dambe ko ka manta? Yadda tayi maganar a cushe ya so ba shi dariya amma sai ya gintse fahimta da yayi so take ta zo da rainin na ta da tayi alƙawarin ta daina ' "Oh i see . Yace yana barin kusa da ita ya koma ga Yakaka wacce ita ma ta tsorata da ganin yadda Fuskar Sofi ta kumbura tayi jawur kamar wacce ta shiga filin dambe da wanda ya fi ƙarfin ta . Bayan ya shirya ya fito gargaɗi ya yiwa Sofi kan kada ta yarda ta fita ko'ina ta zauna ta kula masa da Wafaa . Kafin azahar zai dawo su yi Sallama saboda bayan Azahar zai tafi . Bai yi zaton samun amsa mai daɗi daga gurin ta ba amma ga mamakin sa sai ya ji ta amsa har tana masa fatan alheri hakan sai ya faranta masa tare da ƙara masa kuzari ya bar gidan cike da nishaɗi farin-ciki goma da ashirin . Sai dai yana fita Sofi ma ta fice kai tsaye inda suka yi za su haɗu sa Samy baby domin ta bata cikon kuɗin da za'a yi harkokin aiki kama daga kuɗin jirgi da Samy Baby ta bata tabbacin ta samu wanda zai mata hanya muddin ta saki kuɗi cikin kwanaki uku ma za ta ɗaga India, da yake kan Sofi ya kunce ilmin zamanin ta tare da wayewar ta sai suka gaza yi mata amfani saboda taƙi basu dama shaiɗan da muƙarraban sa kaɗai ta sau wa ragamar rayuwar ta cikin tsakanin jiya da yau ko ibada ta daina yi kwata-kwata da daman dai ba sosai take tsayar da Sallah ba amma daga jiya zuwa yau ko Sallah ɗaya bata yi ba,  cikar mummunan burin ta kawai take mafarki a bacci ko a farke ita dai burin ta ta ga bayan Yakaka "kaicho Sofi . Haka ta ɗau kuɗi zunzurutu naira Miliyan biyar da dubu dari shida ta bawa aminiyar ta Samy Baby bayan naira Miliyan huɗu da rabi da su kenan kuɗin da ke account ɗin ta da tun a jiya tayi transfer su zuwa account na Samira. Wannan farin kudin kuwa kudin duk wasu gwala-gwalan ta ne tare da wani daya na Momy kori da ta amsa Aro bata mayar mata ba duk ta hada su ta sayar ta dankawa Samira kudin.  "Samira dan Allah ki tabbatar kome ya tafi yadda ya dace kin ga Doctor tafiya zai yi to so nake kafin ya Dawo kome ya kammala sai dai ya dawo ya tarar da gawa kawai . "Kar ki damu ƙawata to meye amfanin ƙawancen mu idan ban miki ba ? Ke ce fa Sofiya ? kar ki damu jibi-jibin nan zan bar ƙasar nan ke dai ki kwantar da hankalin ki bana son yadda duk kika bi kika tada hankalin ki kin ga yadda kika koma kuwa? Kamar wata bazaurar Jaɓa . Ɗauke kai Sofi tayi tana jin zagin walaƙancin da Sofi tayi mata a fakaice . Cikin wayencewa Sami baby ta miƙa hannu ta ɗau wayar Sofi da take ajiye a tsakanin su ba tare da Sofin ta hana ta ba tayi wasu 'yan taɓe-taɓen ta a wayar ta ajiye mata daga nan Sallama suka yi saboda Sofi ta ce bata so Doctor Hamza ya dawo bata gida . Haka kowaccen su ta nufi motar ta Sofi ita ce ta fara barin harabar wajen kafin Samy Baby ma ta tada tata motar ta jaa ta cike da nishaɗi ta kama hanya ' Kome ya tafi mata dai-dai yadda ta tsara yanzu abunda ya rage mata kawai shine ta tattara duk wasu abubuwan da ta mallaka a garin Abuja ta cika motar ta ta bar garin zuwa garin Damaturu inda ta zaɓa domin gina sabuwar rayuwar ta . Ita da Sofi kuma daga ta ƙarasa rufta ta a rami kamar yadda ta shirya a jibi kafin ta bar jahar Abuja sun rabu kenan haihatan ah to aina Sofi ta san za ta kama ta ? Sannan ma cikin shirin ta na ƙarshe da zata yi ta san za ta ingiza Sofi ta aikata abunda zai sa ta iya ƙarasa rayuwar ta a gidan Yari da ba zata samu damar neman ta ba ma dan haka ita ta sha kenan ta kuma rufe shafin Sofiya a rayuwar ta "kayya Samira . Lokacin da Doctor Hamza ya dawo gida ya tarar da Sofi a kitchen tana girki ba ƙaramin daɗi ya ji ba dan haka ya saki jiki da ita ya tsaya a kitchen ɗin suka yi 'yar hira yana ta jaan ta da wasa . Ƙarfe biyu dai-dai ya musu Sallama ita da Yakaka bayan ya haɗa su ya musu 'yar nasihar kan su zauna lafiya kafin dawowar su sannan ya ɗau kuɗi masu kauri ya danƙawa Sofi ko za su buƙaci wani abu sai suyi amfani da shi duk da ya san a store da kitchen akwai kome na daga kayan abinci Dauriya Sosai Yakaka ta nuna lokacin da suka masa rakiya bata yi kuka ba sai Sofi ce ma ke zuba masa shagwaɓa wai za tayi  kewar sa shi kuma gaba ɗaya hankalin sa yana kan Yakaka Ko kaɗan ba son ransa bane yayi nisa da ita a dai-dai wannan lokacin sai dai dan ba yadda zai yi aikin sa aikin ceton rai ne dan haka bashi da zaɓi na lokacin da zai yi tafiya a bakin aiki inda za shi ma ceton rai zai tafi dan haka tilas ne tafiyar sa. Haka suka yi Sallama cike da alhini ya jaa motar sa da zai tafi da ita zuwa gidan Doctor Suleiman wanda shi ne zai kai shi airport ya koma da motar tasa gidan shi . Yakaka ita ta bada hanya Sofi ta fara wucewa cikin gidan suna shiga Sofi ta rufe ƙofar ta murɗa ɗan makulli ,  ta ƙasan ido Yakaka ta dube ta Kallon nan da take tsoro shi ta hango a idanun Sofi idan ba gizo idanun ta ke mata ba ma ta ga kamar tana mata wani guntun murmushi. Zuciyar ta ta doka da ƙarfi sum-sum ta wuce ɗakin ta ta bar Sofi a wajen . Kitchen ta shiga a gur-guje tayi girki ta zuba a kula ta bar sauran a tukunya sannan ta jidi ruwan gora da juice ɗin da take ɗan sha ta kai fridge na ɗakin ta ta sa ta dawo ta ɗau abincin tazo fitowa daga kitchen ɗin ta ga Sofi ta tare hanya har yanzu dai wannan kallon ne a idanun ta sannan bata janye murmushin mugunta da take mata ba . Muƙut Yakaka ta haɗiye yawun tsoro . "Mai ciki girki aka yi ne ? Sofi ta tambaye ta fuskar ta a yanayin da bai yi dai-dai da kalmomin da ta furta ba. "Eh nayi girki ne Anty Sofi , naki ma yana tukunya daman yanzu zan zuba miki ' "Bari na kai nawa ɗaki . Sai da Sofi ta mula sannan ta ɗan matsa da kyar Yakaka ta wuce tana shiga ɗaki ta murza ɗan makulli tana jin nutsuwa na safko mata daga nan bata sake fita daga ɗakin ba har dare komen ta a ciki take yi tsakanin banɗaki da tsakar ɗakin Sai wayar ta take yi da Falmata da kuma Lubna da su duka biyun suke cikin watan haihuwar su . Washegari Kamar yadda tayi a jiya haka yau ma tayi girkin ta ta kai ɗaki ta rufe tsawon yinin bata bari sun haɗu da Sofi ba duk kuwa da cewa ta ji motsin ta daga falo . Sau biyu ta samu damar yin waya da Doctor hamza wanda ya shaida mata cewa a gobe zai dawo idan Allah ya yarda dan haka ta ƙarasa yinin ranar cikin nishaɗi da jin daɗin dawowar sa duk da cewa tsakanin jiyan da yau laulayi sosai ya taso ta gaba gadan-gadan kawai dauriya take yi . A washegari da safe Bayan tayi wanka taso fita ta haɗa abin karyawa amma jin yadda Sofi ta ƙure muryar tv tana jin kiɗa ya bata tabbacin tana falon ita kuma cikin kwanakin nan kamar Allah ya ƙara mata tsoron Sofi ne wani irin matsanancin tsoron ta take ji ta yadda ko haɗuwa bata so su yi dan haka ta fasa fita tayi zaman ta kawai a ɗakin da daman ba jin cin abincin sosai take ba yau ta tashi da matsanancin ciwon kai ne . Can kamar hantsi haka tana ɗan taɓa bacci ta ji wayar ta ta ɗau kiɗa , da kyar ta miƙa hannu ta ɗau wayar ganin ƙiran daga masoyin ta ne yasa tayi azamar ɗagawa . Cike da ƙauna da kulawa suka gaisa kafin Doctor Hamza ya shiga rarrashin ta a ƙarshe ya shaida mata cewa dawowar sa a yau ba zata yiwu ba sai nan da kwanaki biyu watau ranar juma'a Wannan karon bata ɗaure ba sai da ta sanya masa kuka da kyar ya iya shawo kan ta tayi shiru da alƙawarin zai dunga ƙiran ta akai-akai duk dai idan ya samu dama . Ba dan sun so ba suka yi sallama saboda  jiran sa da ake yi., duk da cewa ya so yayi magana da Sofi ma domin ya sanar da ita ɗaga dawowar ta shi amma sau uku yana gwada ƙiran ta yana nuna masa cewa tana  amfani/waya da layin nata dan haka ya haƙura ya tura mata saƙo kafin ya kashe wayar sa . Sofi da take baccin asara ƙiran waya ne ya tada ta lokacin da ta ɗau wayar wasu numbers ta gani haka irin na ƙasar waje idan idanun ta sun gani dai-dai ma numbers ɗin na ƙasar india ne dan haka cike da ɗoki ta ɗaga kiran Kamar yadda ta zata ne Samira ce take ƙiran ta daga ƙasar india kamar yadda numbers ɗin suka shaida mata kafin ma ta ji daga bakin Samy Baby . Bata jira sun gaisa ba a ƙagauce ta fara tambayar "Samira kada dai har kin isa india ? Nan Samy Baby tace mata ai ma tana karnataka har kuma ta gana da Boka yanzu haka ma da take jin hayaniya a cikin jirgin ƙasa take kan hanyar ta na komawa masauƙin ta ta kasa haƙura dai dole ta ƙira ta fara mata albishir Boka yace nan da awa biyu zai kammala aikin ta . Wani irin ihun jin daɗi Sofi tayi tana jin kamar an mata bishara da gidan Aljanna. za ta sake yin magana ɗif Samy Baby ta kashe wayar ta . Tana wani murmushin mugunta ta buɗe gidan sim ta zare sim card ɗin ta gutsittsira shi da haƙorin ta ta watsar a gefen hanya ajiye wayar tayi a gefe kafin ta ɗaura seatbelt a hankali ta daga glass na motar kafin ta tayar da motar da bala'in gudu ta cilla ta a titi . Yadda take gudu a titi ba'a ce Mace ce ke jaan motar ba har dai tayi nisa da ainashin garin Abuja tana tuƙi tana bin waƙar da take tashi ta sifukun motar ran ta fes a dai-dai lokacin ji take duniya ta mata daɗin da bata taɓa jin makamancin sa ba ta samu duniya abunda ya rage kawai sai ta miƙe ƙafa domin cin ta . Kafin kamar walƙiya ta ga ɓullowar wasu motoci biyu da gudu da suka yanko daga cikin daji suka yi banga-banga akan titi da yasa ta cikin matsanancin tashin hankalin da ya maye gurbin nishaɗin da take ji ta taka birki ƙuuuuuuu da ba domin Allah ya kiyaye ba da babu abunda zai hana motar tayi ƙundumbala da ita . Samy Baby bata tabbatar yau ita ce rana mafi muni a tarihi rayuwar ta ba sai lokacin da ta fahimci hannun ko su waye ta faɗa' Masu yin garkuwa da mutane ne kidnappers  da take jin labarin su wai-wai sune yau take ganin su a gaban ta kamar a mafarki . Kwakwalwar ta taƙi samun kwanciyar hankalin yin tunani ɗaya kamar yadda idanun ta suka ƙafe ƙaf daga samun damar zubar hawaye duk wasu kalmomi kuma suka ɓace suka shafe daga bakin ta har zuwa lokacin da suka ɗora mata bakin bindiga suka tasa ƙeyarta bayan sun kwashe kome da yake cikin motar suka nausa da ita cikin daji . *** Sofi ji tayi farin-cikin da take ciki ya mata yawan da bata jin za ta iya jurar sa bata ɗan wataya ba dan haka ta ɗau wayar ta da sai lokacin ta lura da saƙon Doctor Hamza . Wani tsallen jin daɗi ta sake yi jin cewa ba zai dawo ba ma a yau sai nan da wasu ƙarin kwanaki wanda hakan duk alamun nasara ne a gurin ta domin kuwa dama ce ta sake samuwa a gare ta . Kiɗa ta kunna a wayar kafin ta buɗe wata 'yar karamar loka da take jikin gadon ta ta fara zaro kwalabe da sauran kayan mayen ta ' Sai da ta tara su jibgi a gaban ta sannan ta shiga ɗaga su ɗaya bayan ɗaya tana tuttulawa a cikin ta tayi ha'in tana jin ta tamkar tafi kowa farin-ciki a duniya tana tangaɗi ta shiga juya jikin ta tana rawa . Daga can ɗakin Yakaka da ta ji shiru babu alamun motsin sofi a falon sai ta lallaɓa ta fito kai tsaye ta tafi kitchen saboda yunwa da ta fara sasuƙar ta har jiri-jiri take ji . Cikin awa guda ta gama irin girkin da take jin sha'awar ci ta kwashe ta kai ɗakin ta ba tare da ta rufe ƙofar ba sai kawai ta faɗa banɗaki tayi wanka ta ɗauro alwala saboda azahar ta gabato. Tun tana wanka take jin ana ta ƙiran wayar ta har sau uku dai-dai da fitowar ta wayar ta sake ɗaukar kiɗa da sauri ta ƙarasa ta ɗaga ta lokacin da ta ga sunan mai ƙiran Falmata ce . "Hello Falmata na kina lafiya ko ? Ko haihuwar ce ? Ko kin haihun ne ? Ta jero mata tambayoyin ba tare da ta ajiye numfashi ba saboda koyaushe cikin bin haihuwar Falmatan take a rai musamman da yake ita ta taɓa haihuwa ta ɗana ta ji yadda haihuwar ke da zafi duk sai take jin tausayin ƙanwar ta kullum cikin addu'ar sauƙa lafiya take mata musamman da cikin na Falmata ya kusan shige kwanakin haihuwar sa da hakan sabon abu ne a haihuwar fari . "Hello Falmata kina jina kuwa ? Ta sake furta hakan cikin damuwa Dariyar da Falmata ta cika mata kunne da ita yasa ita ma ta murmusa tana sauƙe ajiyar zuciya ta ce "meye abun dariyar kina jina ina miki magana wallahi duk kin ɗaga min hankali ganin yadda kike ta ƙirana ina wanka na zo kuma na ɗaga kin yi shiru. "Yakaka bani nake ta ƙiran ki ba wallahi ni yanzu nan na ƙira ina ƙira kuma kika ɗauka . Ɗan jimm Yakaka tayi "to waye yake ƙirana ? Ta tambayi kan ta , sai bata wani damu ba kawai ta zauna a bakin gado suka shiga hirar su ita da Falmata . Sun ɗau tsawon lokaci suna hirar da take sanya su duka biyun a farin-ciki tare da sake ƙaunar juna ' Kafin kamar daga sama Yakaka ta ji an damƙi kafaɗar ta da yasa ta matuƙar tsorata ta saki wayar ta ta faɗi . Jikin ta yana rawa ta miƙe tsaye tana kallon Sofi wacce take tsaye kiƙam hannun ta ɗaya a ɓoye a bayan ta. An-anty Sofi in-ina wuni. Wata irin shashashar dariya Sofi ta saki da hatta Falmata da bata kai ga katse wayar ba ta ji ta . Zuciyar ta ta fara sauya bugu daga lokacin da ta fara saurarar duk wasu zantukan da Sofi take yi cikin maye murya sama-sama . "Kin yi zaton na kyale ki ko ? A tunanin kin shaa da ni kenan ? Ƙaramar kwakwalwar ki ta baki tunanin kin yi nasara ?  Ni Safiya na bari ki rayu da Mijina ki haihu ? "Wacce irin cusashiyar ƙwakwalwa ce da ke ? Ta kifi ? Kin taɓa ganin an yi haka ? Ba zai yiwu ba , ba zai faru ba ba zai taɓa faruwa ba ki zo ki gina rayuwar ki a kan tawa Hamza nawa ne ni Kadai. "Dole na rusa rayuwar ki a duk lokacin da na so , dole ki mutu Yakaka tunda kin ƙi fita a rayuwa ta to zaki Mutu zaku mutu tare da ke da abunda ke maƙale a cikin ki . Wuƙar da take ɓoye a ɗaya hannun ta ita ta zaro wata kakkaifar wuƙa ce sabuwa fil da alama ita ce mafi girma a cikin jerun set ɗin wuƙaƙen ta . Lokacin da Yakaka ta ɗora idanun ta akan wuƙar ta kuma ji abunda Sofi take cewa jikin ta gaba ɗaya sai ya saki kamar an zare mata lakka wani yanayin da ta kasa tantancewa da shi ya shiga bin gaɓɓan jikin ta idanun ta kuma suka kafe akan wuƙar a hankali ta ji kunnuwan ta na toshewa . "Amma kafin na kashe ki zan so na miki ƙarin bayani kan dalilin mutuwar ki zan faɗa miki irin faɗi tashin da na dunga yi dan na auri Mijina da irin son da nake masa , da nasan ke kan ki za ki iya min uzuri akan kashe ki da zan yi . "Tun ranar farko da na gan shi na kamu da son sa , haka na dunga faɗi tashi alhalin ina korar masoyana har nayi nasarar da aka min tsafin da yasa ya fara kulani a matsayin budurwar sa . "Kar kiyi zaton ke ce rai ta farko da na kashe a kan Hamza ke ce ta uku na farkon jariri ne lokacin da aka bani tabbacin idan har ba'a yi mummunan aikin da aka raba tsakanin jaririya da uwar ta ba to babu shakka uwar jaririyar ita ce matar da Hamza zai aura ba ni ba idan kuwa har aka raba tsakanin su za'a kaɗa uwar wani waje mai nisan gaske ni kuma cikin shekarar Hamza zai aureni hakan ne kuma ya kasance . "Na sha wahala kafin na samu wani ɓangare na daga zuciyar Hamza wanda a ƙarshe sai da aka min aikin da aka kashe wani Mijin da zuciyar sa ta mutu a ƙauna matar sa a can ƙasar india bayan duk na sha wannan wahalar ina zaman daɗi da Mijina za ki ratso rayuwar mu ? "Ya kike tunanin ba za ki zama ta uku ba a cikin jerin Mutanen da za su mutu ba ? Dole ki Mutu dole ki zama mutum ta farko da zan kashe da hannu na akan Hamza . Wasu kauraran hawaye ne suka zubo mata kafin ta cigaba da cewa "kin ga laifi na ne ? Ki duba yadda na lalata jikina saboda kawai na burge Hamza na lalata Mahaifata saboda kawai muyi rayuwar hutu da Hamza bana son ko 'ya'yan cikina su ratsa tsakanin mu . Juyowa tayi ta wani irin fisgo Yakaka da daman tuni alhinin Mutuwa ya safko mata bata da wani sauran ƙarfi . Ta gwara kan ta da bango kafin tayi majaujawa da ita a tsakiyar ɗakin ta yasar da ita da wani azabar ciwo ya sarƙe Yakaka yasa ta saki ihun da ya daki dodon kunne Falmata wacce duk take jin abunda Sofi ke cewa.. Ita ma ihun ta saka da ya amsa sashin ta gaba ɗaya da ƙarfi ta miƙe tsaye lokacin da take sakin wayar hannun ta ta faɗi ƙasa tunanin ta yana tabbatar mata da cewa Sofi ta kashe mata Yakaka a yau . Da gudu Hajja da wasu bayun ta biyu suka shigo waɗan da ihun ta ya je har kunnen su Hajja tana shigowa ta gan ta a durƙushe tana murƙususun ciwo tare da ihun ƙiran sunan Allah da na Yakaka cewa take "Yakaka na ta mutu Sofi ta kashe Yakaka dan Allah ku kaini Nigeria . Hajja wacce kallo ɗaya ta yiwa Falmata ta ga alamun haihuwa a tare da ita ita kuma cewa take "To Alhamdulillah abun yau yazo kenan fatan mu Allah ya raba lafiya sannu Uwarɗakina sannu kin ji daure kowacce Mace da haka ta zama uwa daina iface-ifacen nan ikon Allah ke kuma taki naƙudar da ƙiran sunan 'yar uwar ki ta zo miki o wannan ƙauna ta ku ta girmama . Kafin mintoci goma sha biyar labari ya je wa Hajiya Umma kan cewa Falmata na naƙuda nan take ita da kan ta ta taso zuwa sashin . Ƙarƙashin Umarnin Sarki aka fita da ita zuwa asibiti da kawo lokacin Falmata ta daina surutai saboda ganin idon Hajiya Umma sai dai ruwan hawaye da suka ƙi daina zuba mata a zahiri ciwon da take ji a cikin ranta na rashin 'yar uwar ta yafi ciwon da take ji a sassan jikin ta na buɗuwar ƙasusuwan ta sakamakon abunda yake cikin ta da ya shiryawa fitowa duniya a yau . *** Ciwon da ya turnuƙe Yakaka daga ƙasa ya riƙe mata mara shi yasa ta kasa yin wani yunƙuri na kwatar kanta har lokacin da Sofi ta ƙaraso inda ta jefar da ita tana mata wannan kallon da salon murmushin da zuwa yanzu ta san manufar ta ta kuma gane dalilin da yasa take jin matsanancin tsoron Sofi ashe dan ta ita ce ajalin ta Ɗaga wukar Sofi tayi da iyakar ƙarfin ta ganin  haka ya sa Yakaka kare fuskar ta da tafukan ta biyu tana maimaita kalmar shahada a cikin ran ta kamar yadda take jin kome da ya shafi duniya yana shafewa daga ƙwaƙwalwar ta lahira na maye gurbin sa . duhun da yake da alaƙa da tsanantar gudun jinin jikin ta da aikin da ya wuce misali da zuciyar ta ke yi ya safko yana mamaye ganin ta ya koma dusu-dusu take iya hango abunda yake faruwa ta tsakanin yatsun hannunta Ba zata iya tantance mafarki ne ko ido biyu ba lokacin da ta ga kamar an ɗaga Sofi anyi cilli da ita gefe . Doctor Hamza take Iya gani ya gifta ya ɗago Sofi da ta faɗi a gefe. Mari ya shiga ba ta a fuskar ta dama da hagu kafin ya ji cewa marin bai gamsar da shi ba ya shiga ƙoƙarin zare belt ɗin dake kunkumin sa da muryar da ba tayi kama da ta shi ba yake cewa "Sofiya ashe haka kike ? Haka kika min Sofiya ? Haka za ki min ?  Kisa kike ?  daman Sofiya kisa kike yi ? . Ta ko'ina yake zuba mata belt ɗin a jikin ta kafin ya fisge ta su ka fice daga ɗakin ya tunkuɗa ta ta bugu da bango jikin ta gaba ɗaya ya farfashe yayi shatin belt . Ragwab ya zauna akan kujera kamar kuma ya zauna akan ƙaya sai ya sake miƙewa gaban ta ya dawo ya tsaya yana kama goshin sa da hannun sa ɗaya muryar sa na karkarwa yace "Sofiya duk abunda na ji kina faɗa da bakin ki gaskiya ne ? Gaskiya ne ? Kin yi kisan kai kina kuma yunƙurin sake yin wani a cikin gidana duk kuma a dalilina ? Fisgota ya sake yi a inda take yashe tana wani wuri-wuri da ido ko ɗigon ƙwalla babu a idanun ta illa wani irin ƙuna da ran ta ke yi ganin kome take kamar a mafarki . Fisge jikin ta tayi muryar ta a hargitse tana sarƙewa bata cikin hayyacin ta tace " Duk abunda ka ji nace na aikata a ta dalilin ka nayi kuma a shirye nake da nayi abunda yafi haka Wallahi ni Sofiya a shirye nake da na kashe kowa akan ka , idan kuma aka nemi raba ni da kai ta ƙarfi zamu Mutu tare ni da kai zan kashe ka na kashe kaina .....' Wani marin ya daɗa bata kafin ya fisgota Yana tunkuɗa ta hanyar barin gidan yake cewa , "Na sake ki Sofiya Ni Hamza na sake ki saki Uku ki fita daga gidana kar ki sake nuna min fuskar ki har abada na tsane ki . Chak! Sofi ta tsaya ta tirje taƙi tafiya lokacin da kalmomin sa ke mata amsa kuwwa a kunnuwan ta suna zama kamar ɗigon ruwan narkakkiyar dalma a kogon kunnen ta . Zata silale ƙasa ya ɗago ta da ƙarfi ya ƙarasa tunkuɗa ta waje ya rufo ƙofa a fuskar ta da har sai da ƙofar ta bugi bakin ta ya fashe . Wani ihu tayi ta shiga buga ƙofar kamar zata ɓalla da yasa makofta fara leƙowa wasu ma daga sama suke buɗe windows suna leƙen ta . Lokacin da ta fahimci ta zama mahaukaciya sai ta tashi da gudu ta nufi bakin titi ta tare taxi . Tana zama ta faɗi inda zai kai ta kafin ta cigaba da Sambatu cewa take " wallahi ban saku ba Hamza ƙarya kake ni da kai mutu ka raba ahaf ai daga aikin karnataka ya fara ci nan da gobe ma zan dawo gidana Kashe Yakaka kuma ban fasa ba wallahi sai na kashe ta wallahi sai ta mutu.. Ƙiiii mai taxi ya ci birki abinda kawai ya iya cewa shine "Hajiya Dan Allah sauƙa na fasa yin Area da kika faɗa . Haka ta sauƙa bayan ta cusa masa zagin rashin tarbiya da turanci shi kuwa ya jaa motar sa da ƙarfi ya buɗa mata ƙura ' Haka ta taka da ƙafa tana tafe tana surutai a dai-dai lokacin ba wanda zai gan ta ba tare da ya mata ganin mashahuriyar Mahaukaciya ba . *** Lokacin da Doctor Hamza ya koma ɗaki inda ya bar Yakaka anan ya tarar da ita yana share guntun hawayen idanun sa ya ɗago ta ya rungume ta tsam a jikin sa yana jin yadda bugun zuciyar ta ke sassarfa da yasan hakan hatsari ne ga lafiyar abinda ke cikin ta . Nan take ya fara ƙoƙarin bata agajin gaugawa sai dai bisa tilas ya shirya ta suka nufi asibiti saboda fahimta da yayi cewa dole abinda ke cikin ta da bai yi ƙwari ba sai ya fita saboda bakin mahaifar ya riga ya buɗe jini ya fara sauƙa. A can babban asibiti na ƙasa da yake aiki suka mata abinda duk ya dace kafin a mata allurar bacci na ɗan wani gajeran lokaci da ana sa ran idan ta farka firgicin da take ciki ya bar ta . Zama yayi akan kujera yana riƙe da hannun ta ya zubawa fuskar ta ido a can cikin ransa kuwa lamarin Sofi ke daɗa sanya shi a ruɗani a bayan kowacce daƙiƙa yadda yake jin kome kamar a mafarki Wai Sofi ta aikata duk abubuwan da ta lissafa da bakin ta.? Ga kuma ƙwaƙƙwarar shaida nan tana yunƙurin kashe masa Mata da ba domin Allah ya kawo shi ba da babu shakka Wafaa bata raye yanzu a duniya . Sake runtse hannun ta yayi a cikin nasa yana jin ciwon rashin gudan jinin sa da yayi wanda har ƙaunar sa ta fara yaɗo a cikin ransa "Safiya Annoba ce da ya dace ɗan Adam ya nemi tsari da mata ire-iren ta . Maradi Duk yadda likitoci suka yi kokari tare da son ganin Falmata ta haihu da kanta abu yaci tura gaba ɗaya ta gaza yin yunƙuri yadda ya kamata saboda firgicin da ta kasance a ciki ya tafi da duk wani ƙarfi nata . Mafi munin abun shine jinin ta da yake daɗa hauhawa a bayan kowacce minti talatin . Ba hajiya Umma kadai ba har Maimartaba ma ya shiga zullumi da yasa yake ƙiran waya bayan duk ƙaramin lokaci . Dole tasa ya sanar da Biyamuradi Youssouf da bai kai ga sanin Matar sa na asibiti ba saboda a da so suka yi sai ta haihu kawai sai a sanar masa amma a yanzu da lamari ya yi gardama dole aka sanar masa sannan kuma aka shiga addu'a fiye da wacce ake a baya sannan aka ɗaura tukwane domin yin abinci a bayar sadaƙha duk dan Allah ya sauƙi Gimbiya Falmata Matar Yarima Youssouf lafiya . Ganin lokaci zai tafi tare da shiga hatsarin rasa Baby ko uwar yasa likitoci suka nemi da wani makusanci ya sa hannu a shiga da Falmata ɗakin fiɗa . Maimartaba sarki Abdoul-azizou shine da kansa ya zo har asibitin ya sa hannu aka shiga da Falmata ɗakin fiɗa. Anyi aiki cikin nasara an fitar da ƙatuwar jaririyar da ba'a ce ɗiyar fari bace saboda girma zabgegiya da ita jajir mai tarin suma akai kamar an kifa mata hular gashi dan har sai da likitan da ya ciro ta ya sanya almakashi ya yanke mata gashin ta gaban kan ta sannan ta iya buɗe ido . Babu wanda yasan da tahowar Youssoufa kawai sai ganin sa aka yi a asibitin lokacin har an gama aikin an tura Falmata recovery room. Duk suna tsaye suna jiran a fito da ita zuwa ɗakin da zasu Iya shiga su gan ta ɗaya daga cikin manyan malaman jinyan ya fito ya nemi son yayi magana da Youssoufa . Nan yake shaida masa Falmata ta farka amma kuma sai surutai take tana kuka tana ƙiran sunan wata . Ana buƙatar idan zai yiwu waccan ɗin ta zo ko kuma a ƙira ta a waya a haɗa ta da Falmata suyi magana dan kar kuma wata matsalar ta ɓullo . Tare suka koma cikin ɗakin da take abunda ya bashi Mamaki bai wuce nunawa da Falmata tayi ita ba shi take son gani ba Yakaka yayar ta take nema . Shi ba shi da layin wayar Yakaka amma yana da ta Baba Prof , Amnee da Mamar su da yake ƙira akai-akai yana gaishe su da baya zaton ma kawo yanzu sun san Falmatan ta haihu  Dan haka kawai sai ya ƙira Amne Bayan sun gaisa a gurguje ya sanar da su halin da ake ciki na haihuwar Falmata bayan an mata fiɗa da kuma halin da take ciki a yanzu na neman Yakaka . Yanayi biyu ne ya chakuɗuwa Amnee na farko farin-cikin haihuwar Falmata tare kuma da fargabar halin da aka ce Falmatan na ciki bayan fiɗa da aka mata aka cire mata 'yar . Nan take ta tura masa number Yakaka da bai jinkirta ba ya fara ƙiran layin sai dai sau biyar yana ƙira ba'a ɗauka hankalin sa duk ya daɗa tashi ganin yadda har lokacin Falmata bata bar kuka ba . Dan haka ya sake ƙiran Amne lokacin da ta ɗauka ma suna tsakiya da tattauna da khaalty Rahima kan haihuwar da kuma halin da aka ce tana ciki hankalin su duk bai wani kwanta ba. dan haka sai ta haɗa su da khaalty Rahima tayi masa barka ta kuma sake tambayar jikin Falmatan ? Nan yace har yanzu tana kuka kuma Yakaka take nema sannan ita kuma bata ɗaukar wayar . Jin yadda hankalin sa ke tashe sannan ita ma tana iya jiyo kukan Falmatan da take surutai sai ta ce to bari ta tura masa layin Mijin Yakaka ya ƙira shi wataƙila suna tare amma bari a fara sanar da shi Lokacin da ta ƙira Doctor Hamza dawowar su kenan daga Asibitin da yaga ƙiran Amnee ya ɗauka har labarin abunda ya faru ne ya je musu dan haka yayi hanzarin ɗaukar wayar sai dai bayan sun gama gaisawa sai ya ji Amnee ta ɗaura masa da wani batu kan Falmata da ta haihu da kuma halin da take ciki na kuka da neman Yakaka.' Yana jin haka ya fahimci cewa Falmata tana da sani kan abunda ya faru da hakan ne yasa ta firgicin da take ciki a halin yanzu . Amnee ta cigaba da faɗa masa cewa " idan har yana tare da Yakaka to Mijin Falmatan zai ƙira yanzu sai ya haɗa su suyi magana . "To Ya amsa kafin yayi wani yunƙuri Amnee ta katse wayar ta.' Bai rufa mintoci biyu ba sai ga ƙira daga ƙasar Niger. Ɗan jimm yayi kafin ya ɗaga ƙiran saboda sanin da yayi ƙiran daga Biyamuradi Youssouf ne Baban Mama . Lokacin da ya ɗaga ga mamakin sa ba kamar yadda yayi zato ba sai ya ji muryar Youssouf ɗin faran-faran kamar ya san shi haka ya gaisa da shi dan haka shi ma sai ya daure zuciyar sa suka gaisa har ya masa barka . Daga nan sai Youssouf ya nemi da ya haɗa shi da Yakaka , Falmata ce ke son magana da ita. Cikin nutsuwa Doctor Hamza yace "ka kai mata wayar idan ka bata sai na haɗa su  . "D'accord . Youssouf ya amsa yana mai takawa ya matsa gaban gadon da Falmata ke kwance a hankali ya kara mata wayar a kunne cikin taushin murya yana shafa kan ta yace "Mon Bébé ga Yayar ki nan kuyi magana kiji sai hankalin ki ya kwanta ta ki daina kuka . "Hello Yakaka na tace tana shiƙar kuka.. Jin muryar ta yasa Doctor Hamza karawa Yakaka wayar a kunnen ta wacce duk abunda yake faɗa tana jin sa amma bata san da wa yake maganar ba . Jin sautin Falmata tana kuka yasa ita ma kukan ya zo mata sai suka dunga yi tare cikin kukan Falmata ke tambayar ta "Yakaka baki mutu ba ko ? Sofi bata kashe ki ba ? Ashe Sofi haka take muguwa azzaluma  ? Yakaka ki koma gidan Baa kawai idan Sofi ba zata bari ki rayu a gidan ba kin ji Yakaka Dan Allah ki koma Maiduguri kar watarana Sofi ta kashe min ke Yakaka idan ta kashe ki ni kuma ya zan yi.? Doctor Hamza shi ya fara ƙoƙarin hana kukan Yakaka muryar sa a ƙasa yace " Wafaa ki daina mata kuka ta haihu ana so jinin ta ne ya dai-daita a halin da take ciki kwantar da hankali take buƙata ki rarrashe ta . Kallon sa take yi kafin a hankali ta buɗi baki tace "Falmata kin haihu da gaske.? Me kika haifa muna ? Falmata tana goge hawayen ta da bayan hannu Youssouf na taya ta tace "eh Na haihu Yakaka amma ni ban san ma me na haifa ba ban gani ba ma Ya.. Da sauri Yakaka ta katse ta tana cewa "ina abunda kika haifa ? Ki sa a kawo miki ki ɗauki abinki ki riƙe a hannun ki ki rungume ki shayar da shi arziƙi ne babba yau Allah ya miki Falmata kin zama uwa a yau Dan Allah kar ki bari abunda ki ka haifa yayi kuka a domin rashin ki a kusa da shi sa a kawo shi Alhamdulillah Alhamdulillah . Wata irin nutsuwa kalaman Yakaka suka zo mata da shi cikin sanyi murya ta ce "To Yakaka zan sa a bani abunda na haifa yanzu amma Yakaka kina lafiya ko ? Sofi bata yi miki ciwo ba . "Lafiya ta ƙalau Falmata , ki sa a kawo Baby nan ki sa min naji sautin numfashin abunda kika haifa Falmata . "Ina Baby na ? Falmata ta cewa Youssouf haka , ɗan murmushi yayi yana jin daɗin yadda ta fara dawowa hankalin ta. "Riƙe telephoné na amsa miki ɗiyar mu ki ganta Fatima ' Fita yayi sai ga shi ya dawo rungume da jaririyar a hannun sa da shi ma sai yanzu ya ɗauke ta a shirye take tsaf ta sha kayan  sanyi irin na alfarma tayi kyau matuƙar gaya . Ɗora mata ita yayi a jikin ta bayan ya ɗan ɗago mata gadon sai ya zauna tana jingina da jikin sa daga shi har ita tsurawa jaririyar ido su kayi suna ganin tsananin kamannin ta da Mama kamar lokacin da aka haife ta , marabar su kawai wannan tana da girma kuma tafi Mama gashi bayan hakan za'a ce Mama ce kawai Allah ya dawo musu da ita . A hankali ta ɗago ta sumbanci kumatun ta dama da hagu da yasa ta motsawa a hankali tana ɗan yamutsa fuska irin na jarirai. "Yakaka na ɗauke ta ,Yarinya ce mace Mai tsananin kama da Mama , Allah ya dawo mana da Mama Yakaka. Daga can murmushi mai sauti Yakaka tayi tana jin ƙaunar 'yar da bata kai ga ɗora idanu akan ta ba na samun wajen zama na musamman a cikin ran ta a lokacin ji take kamar tayi tsuntsu ta je ta gan ta ta ɗauke ta ta riƙe a hannun ta ta rungume ta a ƙirjin ta ta gwada mata ƙauna a matsayin ta na uwa a gare ta ba wai Yayar uwa ba kawai ɗiyar Falmata ɗiyar ta ce halak malaƙ . "Allah ya raya ta Falmata , Allah ya mata Albarka , Yaa Allah yasa ta amfanar da Al'ummar musulmai ajiye wayar ki ɗaga ta ki shayar da ita anjima zan sake ƙiran ki . "Amin Yakaka . Daga haka Doctor Hamza ya zare wayar daga kunnen ta ya kashe kafin ya jaa ta cikin jikin sa ya rungume ta tsam suna musayar jin ciwon rashin nasu gudan jinin da suka yi . Sumbatar goshin ta da Youssouf yayi bai sa ta janye idanun ta daga kallon fuskar 'yar ta ba da take jin wani abun da ya zarce a ƙira shi da So sannan kuma ya wuce ƙauna tasiri yana bin duk wani sarari na ran ta yana dasa wani al'amari mai girma ji take kamar ta tsaga ƙirjin ta ta sa ta . Wai yau ita Falmata ce take riƙe da 'yar ta ta cikin ta babu shakka Allah shine mafi girman Abun Godiya "Alhamdulillahi Yaa Allah . Ta furta hakan a sarari tana jin wata ƙwallar farin-ciki na cika mata gurbin ido . A hankali Youssoufa ya kai hannu yana ɗauke 'yar daga jikin ta bata yi wani yunƙuri ba illa bin su da tayi da ido cikin ran ta bata mamakin yadda ya iya ɗaukar jariri saboda tun akan Mama ta san ya ƙware . Addu'o'i ya shiga yiwa 'yar sa tsawon mintoci fiye da talatin dan tun Falmata tana kallon su har ta ɗan fara gyangyaɗi . Hannun sa da ya shafa mata kumatu shi yasa ta buɗe ido da kyakkyawar fuskar sa tayi arba yana mata murmushi kafin sautin  sa ya sauƙa a kunnen ta "Mon Bébé kina ji na ? A hankali ta gyaɗa masa kai idanun ta cike da baccin gajiya suke lumshewa sai dai kalmar da ya faɗa ya sa ta wara idanun ta da sauri ta dube shi tana son sake jin me ya ce ? "Wanne Suna kin ka zaɓarwa ɗiyar mu na bar miki zaɓi dan saboda kawai na gwada miki kaɗan dagga farin-cikin da nake ciki. "Da gaske kake ? Ta tambaye shi tana narkar da idanun ta cikin nasa . "Da gaskiya Fatima na bar miki zaɓin sunan ɗiyar mu mai darajja ' " a sa mata Yakaka . Sautin da ya taso daga ƙasan ran ta ya subto akan laɓɓan ta . Shiru yayi yana kallon ta kafin yayi magana ta katse shi ta hanyar cigaba da cewa "indai dai har ka bani zaɓi to a sa mata sunan Yakaka Yayata . "Babu shakka ta cancanta domin kuwa ita ce Mafarin silar haɗuwar sa da Fatima-zahra ba domin ita ba da bai samu Fatima ba bare har ta haifa masa 'yar da yake riƙe da ita yanzu a hannun sa a ƙarshe kuma ita ɗin uwa ce ga 'ya mafi soyuwa a gare shi da har abada baya zaton za'a samu mafiyin ta wajen matsayi a cikin 'ya'ya ..... Tunanin sa bai yanke ba ya juyo yana fuskantar Falmata riƙe da Babyn a hannu yace "Meye Sunan ta na ainashi..? Cike da zumuɗi Falmata tace "sunan ta Amina. Bai ce ƙala ba sai ya sake mayar da kai ga yiwa 'yar sa addu'a kafin bayan ɗan gajeren lokaci ya ɗago kan sa yana mai ɗora mata 'yar a jikin ta yace " Sunan 'yar mu Amina riƙe ta da kyau 'ya ce a gurin ki sannan kuma 'yar uwa. Da hannuwanta biyu ta rungume ta tana jin yanayin da yafi na ɗazu yana danne ta ta kasa tsayar da hawayen farin-cikin da yake sauƙa fuskar ta kamar yadda ta kasa ɗauke ido daga fuskar Amina . Haka ma Biyamuradi Youssouf da yake tsaye akan ƙafafun sa hannuwansa duk biyu a zube cikin aljihun sa yana murmushin da yake bayyana haƙoran sa ya kasa janye ganin sa daga kan su kamar yadda yake jin ƙaunar su biyun tana fisgar sa tamkar wanda guguwa ta riska a tsakiyar rairayin hamada . *** Daga nan ɗakin da Falmata zata cigaba da zama kafin a sallame ta aka kai ta bayan nan Hajiya Umma da har yanzu bata tafi gida ba ta shiga inda suke ta mata sannu sannan ta sake mata addu'a ita da Amina kafin ta bar asibitin . Sai kuma ta fara amsar waya daga Iyaye da dangin ta na Nigeria har dai zuwa lokacin da likitoci suka buƙaci da a bar ta ta samu hutu mai yawa kar a takura ta. *** Daga lokacin da Doctor Hamza ya ga har dare yayi bai ji wani labari ba daga iyayen sa sai ya fahimci Sofi ta rufe zancen duk abunda ya faru bata faɗa ba . Dan haka shi sai ya yanke shawarar sanar da iyayen su da kansa dan haka a daren ranar bayan sallar isha'i ya hada conference call da Baba Prof da Amne da Khaalty Rahima da Momy Kori da shi kan sa Baban Sofi. Bayan duk ya gaishe su sai ya nemi da su bashi dama zai musu bayani. Nan ya shiga basu labarin duk yadda kome ya wakana a tsakanin sa da Sofi tun daga farko har ƙarshe . Kafin ya gama Sallallami da kukan Momy kori tare da Amne ya cika wayar . Sai da kyar Baba Prof ya sa suka yi shiru domin shi da kansa Baban Sofi ya gaza cewa kome kawai kamar ruwa ya cinye shi saboda tsabar shiga razana da muzanta shi da Sofi tayi. Ɗan taƙaitatcen Bayani Baa yayi akan lamarin da ɗari-cikin-ɗari ya goyi bayan hukuncin da Hamza ya ɗauka ya ɗora da cewa "tunda har dai abu ya zama da neman aikata kisan kai to babu shakka ba amfanin zaman rabuwar ita tafi dacewa. Matsanancin kuka Momy Kori ta sa cikin rishin kuka take sanar da su cewa ita har kawo yanzu ma da ake wannan maganar bata ga Sofi da idanun ta ba Sofiya bata zo gida ba to ina ta tafi ? "Ta tafi ko'ina ma Kori , ina mai tabbatar miki da cewa Safiya ba za ta zo ta zauna min a gida ba domin nima ba zan zauna da mashayiya kuma makashiya ba tunda irin rayuwar da ta zaɓarwa kan ta kenan to tafi duk inda za ta tafi tayi rayuwar ta amma ni dai ban amince ta zo gidana Alhaji ka shaida ni na cire Safiya daga cikin 'ya'yana' ku kuma ina mai baku haƙuri kan abunda ya faru ita yarinyar ma dan Allah a bata haƙuri ita da iyayen ta . Daga haka Baban Sofi ya yanke ƙiran daga ɓangaren sa . Duk son kai irin na Momy Kori yau sai ta gaza kare 'yar ta haka tana ji tana gani saki Uku ya tabbata tsakanin Sofi da Hamza sannan kuma dole ta bada haƙuri ga su Amnee da shi kansa Doctor Hamzan da ya rasa gudan jinin sa sannan ta ajiye wayar . Daga nan suka cigaba da jimantawa tsakanin sa da iyayen sa inda Amnee ta nuna son Yakaka ta zo gida a kula da ita amma tun ma kafin ta gama magana Baba Prof ya nuna rashin amincewar sa hujja da cewa ai shi Hamzan likita ne dan haka zai fi kowa lura da ita dole Amnee ta haƙura ita kuwa Khaalty Rahima daman bata cewa kome sai addu'a kawai tayi ta danne duk wata damuwar ta saboda kara . Daga nan aka yanke shawarar cewa jibi Amnee da Zainab za su tafi Abujan daga nan su haɗu da hafsa idan sun duba Yakaka da jiki daga nan sai su dawo Kano su wuce Niger gurin Falmata . Su Hafsa zasu dawo bayan suna Amnee kuma za ta ɗan yi ko da sati biyu ne tana kula da Falmatan . Kafin kwanaki biyu zance ya gama baza dangi kan abunda Sofi ta aikata na yunƙurin kashe kishiyar ta kuma ta gudu ba'a san inda take ba. Amnee sun je Abuja tare da direban su a babbar motar da Amnee ta cika kusan rabin ta da kaya . Sun kwana a gidan Doctor Hamza ta sake rarrashin takwarar ta Yakaka sannan ta bata kayan gyara da tarin wasu turarurruka sannan ta sanar da ita sakon Prof da yace cikin satin nan za'a zo a shirya mata kayan ta a gidan . daga nan kuma sai suka wuce Maradin Niger da tarin kayan ƙamshi da gyaran jiki tare da kayan jarirai masu kyau da tsada  da Amnee tayi tanadin su musamman domin Falmata da zata haihu kayan gyaran tafiyayyu ne daga Chad . Can a Maradi suka ga tarba irin ta saraki sai nan-nan ake da su ana sauƙe musu kabbakin arziki. Daga Zainab har Hafsa sai da suka yi santin kyaun sashin Falmata da irin gatan da ake mata babu abunda yafi burge su irin tarin hadiman da take da su da ko yaya ta motsa sai sun mata sannu girma irin ta sarauta sai gidan sarauta . Lokacin da Yakaka ta samu labarin cewa jaririya Sunan ta ta ci har sai da tayi kuka dan farin-ciki . Doctor Hamza ma ya ji daɗi ya kuma musu fatan Allah ya ƙara musu zumunci a ƙarshe yayi alƙawarin daga ya ɗau hutun sa nan da wasu watanni cikin shekara mai zuwa zai kai Yakaka har Niger ta gano takwarar ta . Ranar suna kuwa Al'umma da suka taru ba'a ce Falmata bata da dangi a Niger ba. A gurin taron suna dangin suka dunga tsurkun tururuwar zuwa duba Hajiya Mama wacce jinya ta sarƙe ta sakamakon wasu munanan ƙuraje da suke feso mata duk a ƙafafun ta bayan hawan jini da ciwon zuciya da suka mata rubdugu bata ko iya tafiya gaba ɗaya rayuwa ta mata juyin waina a tanda . Kowa ya fito daga sashin sai yayi gulmar sakayya ce take gani tun daga nan duniya . Wacce irin ta Maimounatou ɗiyar sarkin Agades ma ta samu sakamakon mutuwa da Mahaifin ta yayi a tun jinyar da ya afkama sanadin mummunan abun kunyan da ta aikata kan yunƙurin kashe Mijinta a halin yanzu kuwa rayuwa ta mata atishawar tsaki batta ga tsuntsu batta ga tarko . 'Yayan Hajiya Mama kansu gaba ɗaya basu da sakewa a cikin taron sunan duk kuwa da cewa sun zo sun kuma kawo kayan jaririya da na uwa irin na alfarma . Da kaya sai da Falmata ta rasa gurin zuba su tsakanin wanda Mijin ta tayi mata da wanda iyayen sa suka mata da wanda Iyayen ta suka kawo mata da kuma na 'yan uwan sa ga kuma na dangi da abokan arziƙa . *** Bayan suna da Zainab da Hafsa da zasu koma kayan niƙi-niƙi aka haɗa Su da shi . Ita kuma Amnee ta zauna kula da Falmata da ta dage tana lura da ita saboda haihuwar da tayi wani ɗam rami na musamman na turara jiki ta sa aka mata a cikin uwarɗakin Falmata kamar yadda al'adar su take su basu cika shan magungunan na mata ba sai gyaran jiki tsaftar sa da ƙyalƙyale fata suka fi bawa muhimmanci . Gefe guda kuma ita ma Hajja ta dage da nata gyaran irin na matan ƙasar Hausa da su kuma suka fi bawa shan kayan ɗa'a muhimmanci . Kafin sati biyu Fatar Falmata ta zama kamar bayan tarwaɗa yayin da wani fitinannan ƙamshi ya zauna mata a jiki 'yar kiɓar shayarwa da tayi ta amshi jikin ta sai ta koma kamar irin hamshaƙan matan nan da suke kan ganiyar ƙuciyar su duniya kuma ta juya hasken ta akan su tana haska su . Bayan cikar sati biyu da kwanaki biyu Amnee ta koma Nigeria inda ta je ta tarar da labari mafi daɗi da Prof ya tare ta da shi kan ya samarwa da ƙanwar sa Rahima Miji . *** Sheikh Mukhtar ɗaya ne daga cikin jerin ƙannen abokansa da bai yasar da zumunci ba ko bayan mutuwar wansa yake ziyartar sa lokaci zuwa lokaci muddin ya shigo garin Maiduguri daga can ƙasar Saudi-Arabia da yake aiki da zama tare da iyalin sa sama da shekaru ashirin da yayi aure. Wannan zuwan nasa lokacin da Prof yake tambayar sa iyalin sa yake shaida masa ita matar tasa ta rasu shekarar da wuce . Prof ya masa ta'aziyya bayan nan ya shawarce shi da kar yayi jinkirin yin wani auren saboda shi aure ibada ne sannan kuma kariya ne . A lokacin Sheikh Mukhtar ya nuna masa cewa har kawo yanzu dai bai samu matar da ta kwanta masa ba wacce ya yarda da hankalin ta da zai iya danƙa mata amanar tarbiyyar 'ya'yan sa da matar sa ta mutu ta bar masa su huɗu . Sannu kan hankali cikin dabara irin ta manya Prof ya gabatar masa da Khaalty Rahima cikin sa'a da ganin girman sa Sheikh Mukhtar ya nuna amincewar sa ɗari bisa ɗari muddin dai ita ma ta amince da shi . Lokacin da aka sanarwa da Khaalty Rahima batun Sheikh Mukhtar bata ƙi ba tunda dai iyayen-goyon ta sun amince ita kuwa me zai ta tayi gardama idan tana da damuwa ɗaya ce ji da tayi ƙasar za ta bari gaba ɗaya ta bar Bulama dan ta sauran 'ya'yan ta mata ta san Allah ya riga ya sanya mata su a hannun nagartattun Mazaje ' Damuwar ta Bulama ne da ya shaƙu da ita fiye da misali sannan babu wani dangin sa na uba da aka samu ɓullowar su har kawo yau duk kuwa da neman da aka ta yi saboda har kawo yau da ake ɗiban shekaru fiye da bakwai da tarwatsa musu gari da 'Yan tawayen Boko Haram suka yi alƙaryar su bata sake kafuwa ba an riga an shafe ta mafi yawan mutanen su kuma sun mutu da take hasashen ciki har da mafiya-yawan dangin Uban su Yakaka da daman ba wani yawa suka cika ba ƙaramar zuri'a ce da su masu gajeran baya . Duk da ba wai shakkun Bulama zai wahala bane idan har ta bar shi a hannun Amnee sai dai tasirin tsakanin uwa da ɗa ne musamman waɗan da suka shaƙu ya haka raba tsakanin su ba ƙaramin abu bane sai ko Mutuwa . Ga jin daɗin ta kuma lokacin da suka yi ganawar farko da Sheikh Mukhtar shi da kansa ma ya mata batun riƙon Bulama zai dawo hannun sa daga zarar sun yi aure . Da yake lamarin ba wai na yara bane cikin satika uku har magana tayi ƙarfi inda nan da satika huɗu mai zuwa za'a ɗaura auren idan ya tashi tafiya nan da watanni biyu ya tafi da Matar sa da ɗan su . Bayan watanni shida. Maradi Niger Siyama tare da Falmata ne tsaye suna Sallama a jikin motar da Biyamuradi Youssoufa yake lafe a ciki yana riƙe da Amina wacce Falmata ta mata laƙabi da ( Ukhtee ) take ƙiran ta haka da kuma sunan ya bi bakin jama'a kowa ma hakan ke ƙiran ta. Jin Sallamar tasu taƙi yankewa yasa Youssoufa leƙo kan sa yana cewa "Siyama kin ka ce yau aikin rana kin ka tahi yanzou kouwa ga hantsi ta ɗagga ko kouwa kin fara wassa ne da aikin naki ko kouma kin gajiya ne za ki bari dagga farawar ki.? Da sauri Siyama ta saki hannun Falmata da ta riƙe jin cewa Biyamuradi Youssouf ya  sako maganar aikin da da kyar yarda ta nema ta fara zuwa har sai da Maimartaba ya sa baki yace aikin ta na ceton rai ne sannan tun tasowar ta burin ta ne ta zama likitar haƙora ƙaƙa zai hana ta bayan shi ya san daɗin samun cikar buri a rayuwa tunda shi ma babu wanda ya katse masa nasa burin na zama Babban Soja mai yiwa ƙasar sa hidima . Ba yadda ya iya haka ya haƙura aka samar mata da aiki a babban asibitin jaha tare da sharaɗin ba ita babu bin sa jaharTahoua sai dai shi zai dunga zuwa kamar yadda suke yi a tun can baya . Babu jaa Siyama ta amince saboda ranta ya afu ga son taimakon Al'ummar ta itama  lokaci yayi da za ta bayar daga ilmin da Allah ya hore mata falalar sa . Baya tayi tana jaan mayafin ta ta rufe cikin ta da ya fara girma da yake nuni da nan ba da jimawa ba Ukhtee za ta samu ƙani ko ƙanwa . "Ƙamnata Allah shi kiyaye mukku hanya hirar mu ba mai yankewa ce ba ina dai sake faɗa miki dan Allah dagga kin koma ecole ki dagewa karatu kiyi zarra ga abokan karatun ki hakan zai zama abun alfahari ne a gare mu. Falmata tana murmushi ta amsa da "Insha Allah ba zan baki kunya ba Docteur Siyama nan da wassu 'yan shekaru ƙamnar ki zata zama diplômée. "Allah shi badda sa'a ƙamna ta. "Amin . ta amsa tana shigewa Mota direba ya jaa suna barin gidan , Falmata ta waigo tana miƙa hannu domin ɗaukar Ukhtee da take ta tsalle a jikin Baban ta tana wasa girman jikin ta da wayon ta sun wuce na watannin ta shidda sai dai a kai ta watanni goma . Noƙewa tayi tana ƙin zuwa ta faɗa jikin Baban ta da sauri tana ƙyaƙƙyala dariya irin ta yaran da lafiya da jin daɗi ya wadace su . A lokaci ɗaya iyayen nata su ma suka sa dariya suna bin ta da kallon dake cike da ƙauna Falmata ta ɗan jaa kumatun ta "Ukhtee yau ni kike yiwa ƙyauya ? Ai anjima kaɗan za ki zo ne . Shafa kan ta Youssoufa yayi wanda ya sha adon ribbons irin na yaran gata da ya dace da lallausar sumar kan ta mai tarin yawa da yake sake fiddo kyaun ta da ido bai gajiyawa wajen kallon ta. "Ki rabbu da ita Fatima kin iya shigga tsakanin ɗiya da Mahaifin ta ? Girgiza kai Falmata tayi tana mai matsowa jikin sa ta kwantar da kan ta ta ɓarin jikin sa na dama ita da ukhtee fuskokin su na kallon juna akan ƙirjin sa . Haɗa su yayi ya rungume bayan ya sumbanci kan Falmata da yake ƙirjin sa. "Fatima-zahra ina son ku irin son da ba shi da iyaka. "Biyamuradi Youssoufa mu ma haka muna ƙaunar ka irin ƙaunar da bata da iyaka. Direban da yake iya jiyo sautin su sai ya ƙara volume ɗin radio da waƙar matashiyar mawaƙiyar nan camelia jordana mai taken mens moi take tashi cikin baitukan ta inda take cewa  : "Je rougis je rougis je rougis Quand tu me souris Ô tes yeux menthols Me mentent et m'affolent "Oh mens-moi si tu m'aimes Mais me manque pas Me manque pas Me manque pas "Je défaille à tes mots fous Mots doux vaudous Quand je suis dans tes bras Hé dis, tu penses à quoi ? Abuja Sofi lokacin da ta bar gida bayan ta ci uwar wahala kafin ta samu ɗan tasi ɗin da zai yadda ya ɗauke ta taje ta sayar da ɗankunnen gwal ɗin da ya rage mata tal a kunnen ta ta biya shi kuɗin sa . Daga nan wani ɗan ƙaramin hotel mai sauƙin kuɗi ya kai ta ta kama ɗaki ta shiga ta zauna a cikin dabarar ta da tayi niyyar ƙullawa na rufewa kowa maganar saki ukun da Hamza ya yi mata har sai zuwa lokacin da aikin boka ya ɗau wuta akan Hamza shi da kansa ta san zai fara neman ta daga nan idan ta gama wana shi ta rama duk irin cin mutumcin da ya mata sai ta nemi da su rufe zancen sakin a tsakanin su kada kowa ya ji su koma su cigaba da zaman su.. Tasha alwashin sai ta walakanta rayuwar Yakaka dan ta ma fasa kashe ta da wuri sai ta mata gashin ƙuma sannan za ta ƙarar da numfashin ta a doron ƙasa.. Kashe wayar ta tayi ta kwanta amma ta gagara bacci saboda tsamin da jikin ta yayi yana mata ciwo na fitar hankali . Dole ta sa ta tafi asibiti aka bata magunguna ta zo ta sha . Daren ranar haka ya ƙare mata tana surutan iska . Washegari kuwa da farar Safiya ta dasa zaman ƙiran Samy Baby sai dai layi ya ƙi shiga wasa-wasa sai da ta shafe tsawon yinin ranar da waya a hannun ta tana ƙiran layin da Samy Baby ta ƙira ta da shi har wayar chaji ya ƙare ta mutu bata samu ta shiga ba Ta lallaɓa ta sayo kan chaja ta zo tasa bata jira wayar ta cika ba ta dasa daga inda ta tsaya wajen ƙiran layin Samy Baby . Kafin cikar kwanaki uku Sofi tayi ƙaramar hauka a ɗakin otel saboda dai babu wani saƙo daga Samy baby babu alamar sa kuma ita ta gagara samun ta sannan kuma ko alama bata ga ƙira daga wani nata ba da da har kashe wayar take dan kar a ƙira ta. Doctor Hamzan da take hasashen aiki ya fara cin sa kuwa duk lokacin da taga alamun Kamfanin Sadarwa sun tura mata saƙo zato take shine . Haka zata yini sambatun ƙiran sunan sa. Kafin cikar Sati kuɗin hannun ta ya ƙare da daman fiye da rabi zama take da yunwa tana biyan kuɗin ɗakin da take kwana . Ala tilas ta fita daga Otel ɗin kawo yanzu kwakwalwar ta ta ƙara birkicewa ta kasa yarda da abun da ya faru da ita yake kuma sake faruwa da ita . Ciwon mazaunan ta da suka ɗuri ruwa tun ranar da ta yanke shi yafi kome ɗaga mata hankali saboda azabar da take sha kullum dare bata iya bacci . Ba arziƙi ta kama hanyar gidan su a birkice kamar sabuwar mahaukaciya . Da zuwa zata sake dasa sabuwar ƙarya ta tarar da ashe tuni kome ya jima da kwaɓe mata asirin ta ya daɗe da tonuwa kowa kuma yasan abunda ya faru abunda ta aikata da irin hukuncin da Hamza ya yanke mata . Babban tashin hankalin ta yadda tana ji tana gani Baban su da ya dawo ƙasar kwanaki biyu da suka wuce ya kore ta a gidan bayan ya ƙare mata tanadi . Gidan wata dangin dangau ɗin Hajiya Kori da take mata kore a can irin unguwannin kusa da ƙyaukan Abuja nan Hajiya Kori ta sa direba ya kai Sofi ba tare da sanin Mahaifin ta ba domin idan ta shi ne kawai Sofi tayi tafiyar ta Momy kori ta ce ta zauna a can kafin Baban ta ya huce ya saurare ta . Bata haƙƙaƙe da babu wata sa'a da ta rage mata a rayuwa ba sai da aka shafe fiye da kwanaki arba'in tana ƙirgawa babu Samy Baby ba labarin ta . Zuwa lokacin ta haƙiƙance cikin biyu ɗaya ne ko dai Samira ta yaudare ta ta mata damfara ta gudu a duniya ko kuwa ta gamu da mummunan hatsarin da ya rutsa da rayuwar ta a can india ba tare da an mata aikin da ta aiketa yi ba . Ƙurunƙus sai gaba ɗaya mummunar zuciyar ta da shaiɗan da bai riga ya gama cika aikin sa akan ta ba suka cigaba da mata raɗa cewar ai babu wani amfanin da rayuwa za ta iya sake mata nan gaba . Dan haka sai kawai ta afkama shaye-shayen miyagun ƙwayoyin da basu cika tsada ba sai mugun aiki dan da haka kaɗai take iya samu ta hasko kan ta a irin rayuwar da ta kwashi shekaru tana tsarawa a kan ta ita da Doctor Hamza. Kafin wasu watanni ta yiwa rayuwar ta illa ga kuma ciwon da yake daɗa cin jikin ta gaba ɗaya ta sururuce ta koma irin mutanen da ƙwaya ta gama musu illa a rayuwa suka zama marasa amfanin da ba zasu iya yiwa kan su ba ma bare su yiwa wani . To ai daman a rayuwa muddin Shaiɗan ya zama jagorar ka ba zai kauce ba har sai ya kai ka tsakiyar kogin nadama da ba kuma za ka iya fiddo da kan ka ba. *** Yakaka da Doctor Hamza kamar kullum suna kitchen da safe suna aikin su tare da dai mafi yawan aikin Doctor Hamza ne ke yi saboda kome Yakaka ta ɗauka za tayi sai ya hana yace kar ta wahalar da kan ta da Babyn sa . Suna gaf da kammala haɗa abun Breakfast ɗin su tattabarun rannan suka sauƙo sai dai a yau su uku ne tare da su da 'yar wata matashiyar tattabara da duk alamu ba'a jima da fara fita da ita kiwo ba. Da sauri Yakaka ta nuna masa su tana cewa "Laa Habibi ka ga tattabarun mu na rannan har sun samu baby ko ba su bane .? Da sauri Doctor Hamza ya mayar da ganin su kan sa yama dariya yace "ai kuwa sune wai har sun haihu ? Gaskiya sun yi ƙoƙari . "Ba dan nima dai ga nawa Babyn yana hanya ba ai da sai nace sun cinye mu a wasan . Dariya Yakaka tayi tana ɗiban 'yar shinkafa ta watsa musu kafin ta taya shi su kwashe abincin karyarwar su kai falo . Bayan sun gama brakfast suka yi wanka Yakaka ta taya shi ya shirya suna yi suna 'yar soyayyar su da ba'a cika magana a cikin ta sai da suka fito za ta masa rakiya yana riƙe da kunkumin ta sannan yace "Wafaa  kin ga na manta har zan fita ban sanar da ke ba ƙanwar abokin aikina da yake nan unguwar ai kin san shi ko Doctor Abdallah ? Gyaɗa kai Yakaka tayi tana jin zuciyar ta na sauya bugu da ba ma zata iya bada amsa da baki ba. Murmushi Doctor Hamza yayi yana mayar da ƙofa ya rufe ya jawo ta jikin sa ya matso da ita Sosai cikin ta ne kawai ya tokare ya hana haɗuwar ƙirjin su . Muryar sa a ƙasa-ƙasa yace faɗa min meye a zuciyar ki na ji ta sauya bugu me kike tunani ? Girgiza kai ta sake yi cike da ƙagautuwa ta ji ƙarshen zance tace "ba kome , habibi me ya faru da ƙanwar Doctor Abdallah ? 'Yar sassauƙar dariya yayi ya jaa karan hancin ta kafin yace " sunan ta Madina ma'aikaciya ce a ƙungiya mai zaman kanta da take bada tallafi ga kasashen da annoba ta fadawa a sakamkon yaki ko na ɓullar cutuka watau NGOs babbar ma'aikaciya ce a kungiyar da bata dade da da dawowa daga... Cike da gundura Yakaka ta Katse shi "Habibi mana to ni meye alakata da ita? Wannan karon dariyar da yake gintsewa ita ce ta bayyana ya shiga kyakyatawa ganin haka yasa idanun Yakaka cika da ƙwalla ta fara ƙoƙarin zamewa ta bar gurin . Da sauri ya riƙo ta gaba ɗaya ya rungume ta a jikin sa yana dai-daita nutsuwar sa daga barin yin dariyar da yake yace "Wafaa aina kika koyi kishi haka un ?? Haka kike sona ashe ? Ki kwantar da hankalin ki Wafaa ni naki ne ke kaɗai da yardar Allah babu wacce zata sake ratsa tsakanin mu ke kaɗai kin isheni rayuwar duniya kin ji ko ? A tare suka yi ajiyar zuciya kafin ya cigaba da cewa "Abdallah shine ya bani labarin ƙanwar sa da shirin da take yi na tafiya Maiduguri domin yin aiki dalilin da yasa ya min zancen domin ya ji yaya lafiyar garin yake ? To bayan na ba shi amsar da ta dace shine har ma na ɗan ba shi bayani akan labarin rayuwar ku yadda kuka kasance a matsayin 'yan gudun Hijira har ma ya sake jimantawa to ashe ya faɗawa ita ƙanwar ta shi sai jiya yake shaida min cewar wai na nemawar Madina izni idan har kin amince tana so ta zo yau ta ɗan tattauna da ke kan yadda rayuwa ta kasance muku a Sanadin Boko Haram . Ya ɗan tsahirta kafin ya ɗora da cigaba da cewa "Wafaa da fatan ban saɓa miki ba da na bada wani ɓangare na labarin ku ba tare da amin.... Da sauri Yakaka ta rufe masa baki da lallausan hannun ta tana girgiza masa kai  tace "Habibi kar kace haka ni wallahi baka min laifin kome ba ina maraba da Madina kace ta zo insha Allah za ta iya samun duk wasu bayanai daga bakina daidai gwargawdon yadda rayuwar mu ta kasance . Sumbatar ta yayi a goshi kafin ya sake ta yana jin yadda take ƙara shiga ransa saboda sanyin halin ta . Daga nan rakiya ta masa ya tafi cike da kewar juna da suke ji a koyaushe idan zasu yi rabo da juna ko da na awa guda ne . Bayan ta dawo cikin gidan da ƙwazo irin nata ta gyara gidan tsaf tana yi tana hanzari tana duba waya dan kar lokacin ƙiran ta kula da Ukhtee yayi . Ta gama ƙarfe tara cif tana zama kuma Falmata ta ƙira ta a skype bayan sun gaisa Falmata tana tsokanar ta Maman biyu sai ta haɗa Su da Ukhtee ita ta shiga lectures. Da kamar kullum idan za ta shiga lectures da take yi a sati sau uku Ukhtee bata yarda da mai rainon ta ta riƙe ta har Falmata ta gama ihu za tayi ta yi tana kuka . Sai fa idan an ƙira Yakaka a Skype an haɗa su nan ne kuma babu ruwan ta da Falmata bare wata mai raino za tayi ta damuƙar wayar tana gwalatu da dariya Yakaka na biye mata tana mata wasa har tayi bacci idan ta farka kafin Falmata ta fito Yakaka za'a sake ƙira ta kula da ita ta waya . Wata irin ƙauna da shaƙuwa ce ta ban mamaki a tsakanin Su biyu yadda Ukhtee ta gane da Falmata da Baban ta haka ta gane da Yakaka haka kuma take son ta . Sai da ta gama mata wasa ta samu tayi bacci sannan suka yi sallama da mai rainon ta ajiye wayar fuskarta ɗauke da murmushi tana jin ƙarin ƙaunar Ukhtee na bin jikin ta "daga an yaye ki zan je na ɗauko ki takwara koda kuwa Baban ki baya so sai dai yayi haƙuri sa samu wasu bayan ke amma ke kam tawa ce 'yata 'yar gidana. Ta furta hakan a sarari dai-dai lokacin da aka ƙwanƙwasa ƙofar gidan. A hankali ta miƙe tana ɗan tura cikin ta gaba da duk cikin watannin sa biyar amma yayi girma sosai "Matar likita ko 'yan tagwaye zata haifa ? Lokacin da ta buɗe ƙofar sai ta ci karo da wata kyakkyawar mace da zata girme mata da kaɗan a shekaru wacce kallo ɗaya tal za'a mata a hango tarin ilmin Boko da wayewar da suka samun wajen zama na dindin a tare da ita bayan hutu da yake numfasawa a jikin ta . Daga kan takalman ƙafafun ta marasa tudu har kan ɗan farin gilashin da yake saƙale akan doron siririn karan hancin suna nuni ne da irin tsadaddiyar rayuwar da take yi ta 'ya'yan gata 'ya'yan manya. "Madina ce . Yakaka ta aiyana hakan a cikin ran ta kafin ta ɗan sake faɗaɗa fuskar ta da murmushi  cikin muryar ta mai sanyin ta ce "sannu da zuwa ki shigo mana . Da taƙaitatciyar Sallama ta shiga gidan kamar yadda fuskar ta ma ke ɗauke da taƙaitatcen murmushi. Bayan sun gaisa Yakaka ta kawo mata zoɓo mai sanyi da yake tashin ƙamshin kayan shai irin na mutan Ndjamena da take ƙamshin ya ɗau hankalin Madina ' Bayan sun ɗan taɓa hira lokacin da Madina take shan Zoɓon da daɗin sa yake ratsa ta "bata taɓa zaton irin wannan local juice ɗin yana da daɗi haka ba , ta aiyana hakan a cikin ranta. Da ta gama sha sai ta fuskanci Yakaka sosai ta sake gabatar da kan ta tare da yi mata godiya da amincewar da tayi ta bata damar tattaunawa da ita . Cikin jin daɗi Yakaka ta ce ita ma tana godiya daga haka shiru suka ɗan yi Yakaka tana ɗan satar kallon Madina wacce take shafa fuskar haɗaɗɗiyar ipad ɗin ta har dai ta kai inda take son zuwa ta ɗago kanta. Fuskar ta a sake tace "Amina zan so ki bani labarin yadda rayuwa ta kasance muku bayan da 'yan tawayen Boko-haram suka tarwatsa garin ku wanne irin tallafi kuka samu daga ƙungiyoyin bada agaji na ƙasa da ƙasa ? shin kun samu taimako ?  sannan a wane hali kuka kasance kafin taimako ya zo muku da kuma bayan taimakon ya riske ku.? Shiru Yakaka ta ɗan yi sannan ta mayar da ganin ta kan kyakkyawan agogon hannun Madina tamkar mai nazarin lokaci kafin ta buɗe bakin ta a hankali cikin sanyi muryar ta tace . "Mafarin Hargitsin Rayuwar mu ya fara ne ni da ƙanwata Falmata sanadin 'yan tawayen Boko haram da suka sa muka tsinci kan mu a matsayin 'yan gudun Hijira. Tammat Alhamdulillah . Alhamdulillahi.Alhamdulillah. Alhamdulillah Godiya ta tabbata Ga Allah Maɗaukakin Sarkin wanda ya bani ikon Farawa da gama litaffin nan da na ɗau tsawon watanni Ashirin da kwanaki shidda  ina rubutun sa tsakanin faɗi-tashi na rayuwar yau da kullum tare da juyin yanayi tsakanin zafi da sanyi da ruwa da iska babu shakka Allah shine abun godiya . Ina roƙon Allah ya yafe min daga abunda ya kasance kuskure na rubutu kasantuwa ta 'yar Adam mai cike da rauni da tarin laifuka ( Allah na tuba ) sannan abunda yake na lada Allah Ubangiji ya karɓa ya ɗora shi bisa mizanin kyawawan aiyukana ( Amin ) Sannan godiya ta marar yankewa ta tafi ne gare ku masoyan rubutu na da baki ba zai iya lissafa adadin ku ba Wattpidians wanda da kuka yi jimirin bibiyar rubutuna tsakanin lokaci mai tsawo da yake cike da tsaiko mai tarin yawa daga gareni , babu shakka ƙauna ce sila kaunar da ku ka nuna ita ta ban ƙwarin guiwar da har ta kai a yau muka kawo ƙarshen littafin tare da ku ,  hakika kalmar nagode tayi kaɗan wajen bayyana muku godiya ta sai dai nace Allah ya saka muku da alkhairi nima Ina ƙaunar ku saboda Allah . Godiya ta musamman ga ƙawa kuma 'yar uwa Fatima Salim aka Batul Mamma da ba domin ita da tarin gudumawa da alkhairin ta a bisa rubutun littafin nan ba da fa tafiyar bata miƙa ba nagode ƙwarai ƙwarai Sister Fatima Allah ya bar ƙauna. Yabo tare da Fatan Alherin ya tafi ne baki ɗaya ga Yayana kuma Malamina Sheikh Muktar Yaa Allah ya saka da alkhairi Yaa Mukhtar kalmar nagode tayi tsororo a tsakanin mu sai fatan Allah ya bar ƙauna . Sannan akwai tarin masoya masu daraja da littafin Mafari ya zama sanadin haɗuwar mu amma ƙaunar mu sai tayi ƙarƙon da ta zarce dalilin haɗuwar Littafi daga cikin su Akwai baki ɗayan jama'ar group ɗina na Mafari fans . Sannan  'Yar uwa kuma jagorata a harkar rubutu Sumayyah Abdulkhadir Takori , tare da ke da dukkanin jama'ar ki na Takorities ina godiya a gare ku tare da ƙaunar ku Allah ya bar zumunci . Jama'ar Batul Mamman na KDM ina godiya da yawan ƙaunar ku . Nafeesa Tafeeda tare da jama'ar ta na Maman Mama novels. Sister Amina Mafari fans Group admin Jameela aka Meela ,Raliya Garba Zulaihat rano , Zahra aka donutfairy ,Maryam Talba ,Auntie Aisha , Fadeela Khabeer godiyar ku ta musamman ce Allah ya bar Kauna. da da da da Masoya haƙiƙa kuna da yawan da ya wuce fa na ƙirga ku musamman dai da yake ai kun san ƙyuiya irin tawa ah to da ya muka sha a rubutun ma ? Lol. Masoya ga dama ta samu na tattaunawa akan duk wani abunda na rubuta daga farko har ƙarshen littafin Mafari . Ga masu min gyara ko domin gaba ina maraba . Ga masu ƙorafi domin gaba ina maraba . Ga masu neman ƙarin bayani/tambayoyi kowanne iri muddin b