[7/14, 1:00 PM] Abue Saleh AlQuyraemey: 🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄 MACIJINE SHI🪱🪱🪱 Na mammy kabeer (Anty mammy) Elegant online writers📚📚 Free book Page 1 Bismillahir rahmanir rahim, Ina godiya ga Allah daya bani damar fara wannan littafi, bayan kammala littafin soyayyata. kasa yadda na fara lafiya naga bayansa lafiya ameen. Gargadi banyarda wani ko wata ya juyamin wannnan littafi ta kowace sigar ba. _______________Wata kyakkyawar yarinya na hango sanye da kaya irin na Fulani, wato rigar saki da kuma zaninta, duka duka rigar da kadan ta wuce cibiyar ta, saidai kuma ta daura zanin da ya rufe mata cikin nata ta yadda ba wanda zai ga jikinta awaje. Farace irin mai sirkin yallow -yellow din nan, tana da doguwar fuska mai kyan tsari dauke da dogon siririn hanci har baka, bakinta dan karami kamar gidan tsutsa, tana da irin manyan idanunnan masu kamar tana jin barci, ga gashin ido zara -zara. Girarta kuwa, kamar wacce aka dora Mata ita dan saiti, gaban goshinta wasu yan kananan gashine kwance lub lub kamar na jarirai. Masha Allah yarinyar ta ko ina ta hadu, dan doguwace marar jiki saidai fa Allah ya hore mata hips Kai kace wata babbar macece Sannan akwai alamun girma akirjinta, ma'ana dai akwai dukiyar Fulani da suka fara tasawa akirjin nata. Duka duka wannan yarinyar bata wuce shekara 15/16 ba, amma kallo daya zaka yi mata kasan Allah yayi halitta agurin. Sandace irin ta Fulani ahannunta tana dagawa sama, da alama tana son hada kan wasu tarin shanu ne dake kiwo cikin wani kayataccen jeji, dan kuwa ciyawace agurin Kore sharr da ita, shanun suke ci abinsu . Tafiya ta farayi gurin shanun dake dan nesa da ita, dan ita tana daga jikin wata bishiya ne tana kallon yadda suke kiwo abinsu. Kanta ta daga ta kalli yadda garin ke hada wani irin hadari baki kirin dashi, kuma da alama koda yaushe ruwa na iya saukowa. "Kuzo mu tai gida abokaina kada ruwan nan ya sauko ya taba mu, don aradu banin son nai mura" Cikin Yaren fulatanci take musu magana, tana daga sandarta. Aikuwa kamar wanda suke jin me take fadi suka fara yin hanyar gida . Murmushi tayi tana mai binsu tana kara daga sandarta sama sabo da suyi saurin karasawa gida. Tafiya suke cikin jajen ita kadai daga ita sai wadannan garken shanun, sam ba alamun tsoro tattare da ita, sai yar wakar tama take tana cigaba da ɗaga sandarta sama. Kusan tafiyar minti biyar sukayi, sannan na fara hango bukkokinsu dake can gaba kadan . AHankali annurin dake kan fuskar yarinyar ya fara dusashewa tamkar yadda hasken rana kan dauke a lokacin a ta zo faɗuwa. Nan da nan damuwa ta maye gurbin nishadi da take, sosai naga jikinta yayi sanyi har suka karasa wata bukka dake farkon rigar da alama nan ne gidansu. Garken shanun ta fara zuwa ta daure su tsaf sannan ta nufi cikin gidan dauke da sallama. Lokacin har anfara yayyafi . Ba kowa a tsakar gidan nasu, hakan yasa ta sauke ajiyar zuciya tare da nufar wata bukka cikin sauri. Saidai kafin ta karasa kofar bukkar aka daka mata wata uwar tsakar da saida sandar hannunta ta fadi kasa. Afirgice ta juyi jikinta na rawa sosai kamar dan mazari, da sauri ta karaso gurin matar data daka mata tsawar "Gani gwagwgo" ta fada cikin rawar murya. Ni kuwa sai na kalli matar duk da cewar farace amman kuma kazanta da rashin kulawa yasa tayi wani irin baki baki fari fari, sannan tana da jiki sosai sam fuskar ta ba alamun rahama a cikinta. Tana tsaye a kofar bukkar ta tana hararar yarinyar dake durkushe gabanta. Cikin masifa da bala'i matar ta fara magana da hausarta marar kyau. "Da kake kokarin shigewa dakin, ubankane zai debi ruwan? Ko kin ajiye bawanki ne a gidan? matar ta fada cikin zaro ido. Kan yarinyar akasa jikinta na rawa ta fara magana "Allah hukkumu hakuri gwagwgo naga ruwa na dan sauka ne shiyasa ban deboba" ta fada cikin rawar murya gami da tsoro. Wani wawan mari matar ta kai mata cikin rashin imani da tausayi cewar yanzu ta dawo daga kiwo kuma ko abinci bata ci amma take kokarin sake turata rafi. "Shegen yaro mai bakin hali wllh yanzu dole ki dobo min ruwan nan dan ubanki karuwa kawai" matar ta fada tana mai hankade yarinyar cike da rashin imani. Faduwa tayi sosai hannunta ya bugu da wani dutse dake ajiye tsakar gidan da alama na zama ne. Kara ta saka cikin azaba tana mai dafe hannunta dake mata wani irin azabar raɗaɗi. "Wayyo handi ɗin boni lalashewa gwagwgo hannu na ta ɓalle" ya rinyar ta faɗa cikin azaba. "Shege wllh dama zai karye danafi kowa jin dadi yarinya kamar aljana, ace kinfi kowa kyau arugarnan? Na tsaneka fattu saina bata wannan shegen fuskan naki, ni maza ki tashi kona shakeki agurin ki mutu kowa ya huta" cewar matar cikin bala'i da tsantsar nuna tsana ga Fattun. Cikin hanzarin ta mike ta zari wani bokitin roba ta fice tana kuka mai tsuma zuciyar ga duk wani mai tausayi. Tafiya mai nisa tayi kafin tazo rafin, har zuwa lokacin kuka take hannunta sai zogi yake mata, ruwan ta debo cikin sauri dan kuwa ruwan da ake ya fara karfi. Saidai me ? tana juyawa tayi arba da wani murtukeken maciji katon gaske ya fasa kai yana huci. Wani irin mugun tsorone ya kamata nan da nan jikinta ya kama rawa har batasan lokacin da bokitin ya fadi kasa ya fashe ba. Tashin hankali kenan wanda ba'a sa masa rana, iyakar ruɗewa da tashin hankali yarinyar nan ta shiga. Hannu ta ɗora aka tana mai kara ƙarfin kukanata. "Wayyo ni fattun bukar na mutu na lalashe ya zanyi da rayuwata mashici zai karni wayyo baffana! wayyo Allah! A taimaka min" Ta faɗa tana kallon botikin nata wanda ya tarwatse a kasa, dama kuma rana ta gama cin ubansa. Shi kuwa macijin nan ganin yadda ta tsaya tana kallon sa kuma tana kallon fasashshen bokitin dake kasa, sai yaga kamar neman makami take dan haka afusace yayi kanta da mugun nufi. Ihu ta kwalla mai karfin gaske tare da zubewa agurin sumammiya dan ganin yadda macijin nan yayi kanta baki bude don hakan ba ƙaramin tsorata ta yayi ba . A Dai dai wannan lokacin ne kuma wani katon macijin ya nufo wannan macijin da gudun gaske, yana zuwa ya sarkeshi suka fara kaiwa juna sara. Hakan shi ya hana wannan katon macijin ya sami damar karasawa inda fattun ke kwance asume. Sosai macizan nan ke kaiwa junansu sara suna murdewa cikin jikin juna, ko wanne yana iya ƙoƙarin wayen ganin ya illata dan uwansa. Ahankali fattu ta fara bude idanunta da sukayi mata mugun nauyi tana kuma lumshesu, hannunta ta daga da nufin dafe kan nata, saidai wani azababben zafi da radadin ga wani irin zugi dataji hannun yana mata, shine ya sanyata sanya kara tare da fashewa da kuka. "Washhhh hannuna wayyo kaina" ta fada cikin kukan tana mai dafe kan nata da dayan hannun marar ciwon. Sai kuma ta zabura cikin azama ta zauna tana mai zare idanu da rarraba su, sakamakon tunowa da katon macijin da yayo kanta dazu. Sai dai koda ta kai duba ga inda macijin yake sai ta hangi macizan sun zama biyu suna ta artabu, gaba daya sun jima kansu ciwo jini yana ta zuba akikkunansu, amma duk da haka sunki daina fadan. Tsoro, fargaba, tashin hankali gami da rudewa suka saka fattu kurma wani uban ihu tare da yunkurawa ta falla da mugun gudu tana ihu cikin rudewa dan ganin macizan sun zama biyu wato har fada suke akan waye zai cinyeta kenan. Duk da irin ruwan da ake zugawa mai ƙarfi ga iska, a haka tayi ta cin uban gudu ko gabanta bata gani ikon Allah ne kawai ya kawota gidansu lafiya. Kai tsaye ta danna cikin gidan da gudu ta shige dan dakin dayake amatsayin nata, cikin rawar jiki ta janyo wasu karare dogaye guda hudu ta kara a kofar, dan sune ke a matsayin murfin kofar tata. Dakin ba komai sai wata yar yaloluwar taburma, wacce kallo daya mutum zai yi yasan cewa taga duniya, dan gaba daya ta ciccinye kuma tayi lakwam da ita. Sai wani zani dake gefe daure, da alama kayan sawarta ne aciki. Tana tsaye atsakar dakin, har lokacin jikin ta rawa yake, ga ruwa sai zuba yake ajikinta yararara!!! Kallo daya zaka mata kasancewa afirgice take sai kif-kifta ido take tana kallon kofa, domin gani take kamar macizan nan zasu biyota. Tayi kusan minti biyar acikin wannan halin, kafin ta fara cire kayan jiki ta dake yararin ruwa "Masha Allah nace, sakamakon ganin wani uban dogon bakin gashi mai santsi akanta lokacin da take zame dan kwalin dake bisa kanta, an raba kan biyu an daure ko wanne bangare sai kuma aka nannade ko wanne a barinsa ya zama kamar gammo, wanda hakan da akayi shine ya hana mu ganin gashin nata tun farko. Zanin dake ɗaure a jinkinta ta kwance ta dauko wani zanin irin wanda ta cire da rigarsa, saidai kayan fa sun sha jiki sosai, sun kode sun jeme sunyi wani fari tas da su, sai wata hula baka irin ta sanyin nan ta dauko ta ajiye kusa da kayan, sannan ta mike tsaye ta cire rigarta ta ajiye ta gefen tabarmar, ahankali ta warware tsangalallen zanin shima ta ajiye gefe, ya zama daga ita sai wani kodadden pant Wanda kana gani kasan shima yaga rayuwa. Kallonta nayi tun daga sama har kasa kawai sai na kuma cewa Masha Allah a karo na biyu domin dai sura kam Allah ya halicce ta agurin fattu dan jikinta har wani sheki yake kamar yar masu kudi wacce ke rayuwa cikin jin dadi. Haka ta dauki kayan ta saka ajikinta tanayi tana kuka abin gwanin ban tausayi. Bayan ta kammala sanya kayan ne kuma saita dauki wanda ta cire ta matse sannan ta makalasu ajikin karan dake jingine akofar dakin nata. Zama tayi akan yar tabarmarta ta dukunkune jikinta tana kuka. Abubuwa dayawa ke damunta ahalin yanzu, na farko tsantsar tsoron macizan data gani dan bata taba ganin irin wadannan macizan ba, domin dayan jikinsa mai matukar shekine da kyau, sai kuma hannunta dake mata azabar ciwo uwa uba ga kuma yunwa da ta addabeta, dan rabonta da abinci tun karin safe da tayi shima nono ne kawai ta sha, har kawo yanzu da magriba tayi bata sake saka komai a bakin salatinta ba. Sosai take tausayi rayuwarta, tabbas rashin uwa babbar gibine a rayuwa, yanzu da innarta na kusa da ita, da tuni ta rungumeta ta fada mata damuwarta, amma rashin dace ta daya shine sam batasan koda fuskar innar tata ba, sannan tana raye ko ta mutu Allah shine kadai masani. Tana cikin wannan hali ne taji an ture karan data rufe dakinta da shi. Azabure ta mike tsaye tana shirin sanya ihu. "Ke fattu nutsu mana nine fa, nine baffanki" wani dattijo ne fari dami da dan tsayi yayi maganar, yana sanye da riga da wando na wani yadi mai arha sai takalmin sau ciki na roba a kafarsa, da hula irin mai malafar nan. Ya shigo cikin dakin da wani kwano riƙe a hannunsa. Ajiyar zuciya ta sauke sakamakon ganin baffan nata, da sauri ta karasa kusa dashi tace "Baffan usee wollahi na tsorata ne" ta fada idonta akan kwanon dake hannunsa. Murmushi yayi yace "Hoo fattu akwai tsoro, sannu maza karbi wannan tuwon ka shinye nasan kanajin yunwa, kayi sauri kar hansai ta gani" yana gama fadin haka ya mika mata kwanon yayi saurin fita daga dakin, dan kar matar tasa ta fito ta ganshi ya shiga uku. Cikin sauri - sauri fattu ke cin tuwon nan kamar zata kware, tas kuwa ta cinye ta side kwanan, sannan ta fice da sanɗa har takai tsakar gidan ta wanke kwanon ta ajiye dakin girki sannan ta sha ruwa tayi alwala ta koma dakinta. Sallar la'asar tayi da magrib dan tuni an kira magriba. Har zuwa lokacin ruwa ake saidai bai kai ƙarfin na farko ba. Tana zaune cikin zullumin matakin da gwogwgo zata dauka akanta, na fasa mata bokitinta da tayi, a haka har akayi isshai tayi salla sannan ta kwanta tana mai karanta addu'a, nan da nan barci yayi gaba da ita, har baffanta ya shigo ya duba ta yaga tayi barci addu'a yayi mata cikin tausaya wa halin kuncin da take ciki sannan yayi saurin fita. Gwagwgo kuwa tana daki ita da yaranta suna ta hira suna cin gyada, ba ruwansu da wane halin fattu ke ciki, shin ta dawo gidanma ko yaya taci abinci ko bata ciba? Sam ba wanda ya damu, kuma ba wanda yayi Sallah a cikinsu. Can cikin dare Fattu na barcinta sai dai cikin damuwa da tsoro take yinsa domin kuwa mafarkin macijin nan take, saidai kuma ba na farkon bane yazo mata yanzu wannan mai kyakyakywan jikin nan ne, amman gaba daya jikinsa jini yake zubarwa, ga wani irin hayaki da tururi dake fita ajikinsa, sai burkima macijin yake yana wani irin kuka da wata murya mai amon sauti, kuma yana nufota da ƙoƙarin hawa jikinta . Wani razanannen ihu ta kwalla tare da mikewa zaune afirgice, tana mai waige waige, ba abinda take iya gani saboda duhun dakin, hakan yasa tayi saurin komawa ta kwanta tare da karanto adduoi kala-kala, hannu ta mika dan janyo zaninta ta rufe jikinta dashi, saidai kuma hannun nata taji ya sauka akan wani abu mai dan karen sanyi da santsi. Cikin tsoro take shafa abun dan jin ko menene, tabbatas MACIJINE dan kuwa ta tabo har kansa .... Masu karatu badai macijin ne ya biyo fattu da gaske ba? Wane hali fattu zata shiga ? Muje zuwa yaki ce dai anty mammy Mrs babi💘💘💘 Share and comment fisabilillah. More comment More typing. [7/14, 1:01 PM] Abue Saleh AlQuyraemey: MACIJE NE SHI 3/4 🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄 MACIJINE SHI🪱🪱🪱 Na mammy kabeer (Anty mammy) Elegant online writers📚📚 https://www.facebook.com/groups/2803452939899949/?ref=share Free book Page 3/4 ________________Cikin tsoro take shafa dogon abun dan jin ko menene, tabbas MACIJINE dan kuwa har kansa ta taɓo. Aikuwa da hanzari ta janye hannunta cikin kidima ta fara ja baya tare da fasa wani irin gigitaccen ƙara, "Wayyo Allah baffa maciji! maciji!! maciji!!!" Gaba ɗaya ta kidime abinda take iya faɗi kenan jikinta na rawa kamar ɗan mazari. Allah Sarki baffa dama ba wani barci yake yi ba, dan yana kula da ɗakin fattu, kasancewar ɗakin yana gaf da ƙofane, dan haka jin ihunta da yayi, yasa shi tashi agigice ya nufi ɗakin nata. Haskawa yayi da tocila can ya hangota jikin bangon ɗakin ta duƙunƙu ne tana ta ihu, da alama batama cikin hayyacinta. Da sauri ya nufeta yana kiran sunanta" fadimatu! ke fadimatu menene? Ya isa haka gani akusa dake baffanki ne kinji daina ihun " Baffa ya faɗa cikin ƙasa ƙasa da murya dan kada ya ƙara tsorata ta. Ita kuwa gaba ɗaya ta rikice kawai kira take "Baffa maciji zai sareni Baffa wayyo Allah na" Ganin halin da take ciki ne yasa Baffa ya fara tofa mata addu'a, cikin minti biyu kuwa tayi shiru sai rawa da jikinta keta famanyi, ahankali ta daga kanta ta sauƙe kyawawan idanunta akan baffan nata, kawai saita saki kuka tana mai cewa "Baffa MACIJINE yake son ya sareni aradu da idonsa na ganshi anan" ta faɗa tana nuna masa gurin dataga macijin. Kallon gurin baffa yayi, shifa ba abinda ya gani agurin, kawai yana tunanin ko mugun mafarki tayi ne, dan haka cikin ƙokarin kwantar mata da hankali yace "shike nan fattu ya tafi maza koma ki kwonta kiyi addu'a Insha Allahu ba bu abinda zai sameka kinji" ya faɗa cikin yanayin Hausar su ta Fulani. Cikin kuka take girgiza masa kai "Aradu baffa dawowa zaiyi tun daga rafi suke son cinyeni fa, bazan iya kwonshiya Ni kaɗai ba" ta ƙarasa tana mai matsowa kusa da baffan. Shiru yayi yana tunanin mai ya kamata yayi, dan gaskiya yaga ta tsorata da yawa, dan haka cikin ƙarfin hali yace "Tashi muje gurin Hansai saiki kwonta shan ko" ya faɗa cikin tausaya wa. Ai kafin ma ya rufe bakinsa ta kai ƙofa, dan ita kam babban burinta ta bar ɗakin nan, tama manta da gurin wa baffan yace taje. Ahankali baffa cikin ɗan tsoro yake tura murfin ɗakin na hansai harya buɗe shi duka. Ya taddasu suna kwance abinsu kan gado ita da yaranta su uku, na miji ɗaya sai mata biyu Dukansu basu kai fattu shekaruba, da alama na mijin zaiyi shekara sha uku, matan kuma basu fi sha daya ba. Kuma dan rashin tsari irin na goggo Hansai da ita da yaranta duka suke kan gadon kuma na mijinta. Ahankali baffa ya karasa yana dan bubbuga fillon da hansai ke kwance, sai uban munshari take zabgawa, banda wari ba abinda dakin keyi. "Hansai! Hansai!!" Baffa ya faɗa cikin Muryar tsoro, dan yasan idan ta farka sai tayi masa bala'in ya tashe ta tana barci. Juyi tayi tare da goge yawun barcin dake zuba abakinta taci gaba da barcinta abinta. A hankali ya fara kiran sunanta da ɗan karfi "Hansai ! Hansai!!" Har sau biyu. Buɗe ido tayi ahankali ta sauke su akan baffa dake tsaye, buɗe idon tayi sosai cikin bala'in ta tace "To jarabarce ta motsa haka da cikin dare zaka zo ka dameni? to wllh garama ka koma inda ka fito dan ba abinda zaka samu agurina, wannan jaraba dame tayi kama, ko sati biyu bakayi da saukemin jarabarka ba shine yanzu ka ƙara jajiɓo jiki kazo ka sake ko? To wllh banda lokacinka kaficemin daga ɗaki" ta faɗa cikin masifa tana mai juya masa baya. Girgiza kai yayi cikin jin kunyar fattu, dan yasan taji abinda gwogwgo take faɗi, kuma ai ita ba yarinya bace bare ace bata san me hakan ke nufi ba, tunda tana karatun addini. Cikin sanyin murya yace "Ashsha Hansai ba wannan ta kawoni ba, dama ina neman alfarmar fattu ta kwana anan ne daku, dan bazata iya kwana ita kadai ba, atsorace take "ya faɗa cikin shakkun zata amince ko yaya. "Kan ubannan yau kuma da wannan sabon munafurcin kuka zo? Fattu ta kwana a ɗakina, lallai in baka mutu ba zakaga ikon Allah, da can da ubanwa take kwana? sai yau zakace ta kwana aɗakina? yarinyar mayya wato cikin dare ta lashemu ko? kai baka da asara, To, ku ficemin aɗaki Allah yasa abinda yake tsoratatan ya cinyeta ta mutu kowa ya huta "tana gama faɗin haka ta juya taci gaba da barcinta. Sosai maganganunta suka ɓatawa baffa rai, saidai bashi da damar magana, kai kawai ya girgiza yace "Muje Fattu" Kuka sosai fattu keyi na tausayin su ita da baffanta ga wannan matsalar dake ƙoƙarin Kunno mata kai, basu da gata sai Allah kawai. Suna fita baffa yace "shiga ɗakina ki kwanta fattun, ni bari na je ɗakin naki kinji" ya faɗa cikin sanyin murya. Girgiza kai tayi tace "Baffa Zan koma ɗakin nawa In kwanta kaima kaje ɗakinka, idan gwagwgo tasan na kwana aɗakinka yanka ni zata yi, dan ta hanani shiga ɗakin" ta faɗa tana mai share hawayenta tare da nufar ɗakin nata gabanta naci gaba da bugawa. "Kiyi hakuri fattu komai yana da iyaka kinji, Allah zai miki sauyi na alkairi" Baffa ya faɗa yana mai mika mata tocila ya ce ki haska ki kwanta kinji, sannan kada ki manta da yin addu'a" Karba tayi tare da ɗaga masa kai ta koma cikin ɗakin. Daga bakin ƙofa ta tsaya tare da haska ɗakin ko ina, ba abinda tagani aɗakin, hakan yasa tayi zamanta bakin ƙofar ɗakin da tocilan ɗin ta ko yaya taji motsi saita zabura ta haska . Sam awannan daren bata sami damar runtsawa ba, ga sanyi da garin ya ɗauka sakamakon ruwan da aka zabga jiya. Sai gabannin asuba sannan barci ɓarawo ya saceta. Wani irin azababben sanyi daya ratsa ƙasusuwan tane sakamakon ruwan sanyin da gwagwgo ta kwara mata, shine ya sanyata zabura ta miƙe da sauri tana haki, kafin ta gama dawowa cikin hayyacinta kuma taji duka yana sauƙa ajikinta ta ko ina, ihu ta fara tana neman taimako amma ba wanda yazo dan taimakon nata, dan baffa yana masallaci kasancewar shine limamin rugar. "Wayyo Allah na gwogwgo kiyi haƙuri wllh bazan ƙara ba, tsautsayine yasa na fashe miki bokati, dan Allah kiyi haƙuri gwogwgo" abinda fattu ke daɗi kenan cikin azaba dan ko ina na jikinta ciwo yake mata barin ma hannunta daya kumbura sosai, alamun tayi targaɗe a hannun kenan. "Wllh yau saina kasheni Shegiyar yarinya muguwa kafin baƙin cikinki ya kasheni, na Tsaneki fattu bana ƙaunar ganinki arayuwata, kinsan nawa nasai bokatin nawa? kika je kika fashemin shi? Murtala huɗu da naira goma fa na siya, wllh saina dakeki, kuma ki sani duk inda zaki je ki samo min kuɗin bokatina sai dai kije dan bazan ɗauki asarar ba" gwogwgo ta faɗa tana haki, kuma bata daina jibgar fattu ba, kamar ta sami jaka. "Wayyo gwogwgo dan Allah kimin rai hannuna zai karye, wllh bada gangan na fashe miki bokati ba, macizaine suka biyo ni zasu cinyeni shine na gudu amma bada gangan nayi ba wllh" ta faɗa cikin azaba dan tuni ƙarfinta ya kare ko iya ɗaga hannunta bata yi. "Allah ya tsine muku keda mashizan shegen yaro karuwa, ina ruwana da macizai? dama sun cinyeki kowa ya huta mai baƙin hali marar farin jinin da kika kasa auruwa, dama shegun macizan sun.......kasa ƙarasa magannarta tayi sakamakon wani ƙaton abu dataji ya faɗo kanta jifff !!! kamar buhun hatsi. "Wayyo ni Hansai menene wannan ɗin yake zagayemin jiki? ta faɗa cikin firgici da tashin hankali tana mai jefar da iccen hannunta. Aikuwa carab idanunta suka sauka akan wani ƙaton macijin daya nannaɗeta ko motsi bata iya yi, kuma ya fasa kai a saitin fuskarta sai huci yake yana fito da harshe. "Wayyo Allah na ni hansai yau me zan gani ? na shiga ukuna malam kazo fattu ta min ture maciji zai kasheni ka taimakeni, handi ɗin bonu lalashewa ni yar nan wayyo malam" ta faɗa cike da tsananin tsoro gami da razani da ƙyar take magana dan ba ƙaramin shaƙar mata jiki macijin yayi ba har wuyanta. Tsoro, fargaba da tashin hankali sune suka daɗa kashewa Fattu jiki, dan faɗuwa tayi ƙasa warwas ko motsin kirki bata iya yi, shikenan Tata ta ƙare yana gamawa da gwogwgo tasan kanta zaiyo, Allah Sarki innarta, yanzu shikenan haka zata mutu bataga innarta ba, batasan ya fuskarta take ba? bare tasan dangin innarta? Amman Gara ta mutumma ta huta da wannan baƙar azabar da take sha agurin gwogwgo. Shikuwa macijin nan ƙara matse gwogwgo yake sosai, gaba ɗaya ta fice daga hayyacinta, dan ko magana ma ta kasa, sai idanunta da suka kada suka yi jajur da su, sai faman nishi take numfashinta na ƙoƙarin ɗauke wa. Saida macijin nan yaga gwogwgo bata motsi alamun ta suma, sannan ya sake ta ta hanyar janye jikinsa daga gareta. Da gudu kuma yayi kan fattu wacce ke kwance cikin tashin hankali ganin yadda macijin nan ya kashe gwogwgo. Runtse ido tayi da mugun ƙarfi tana salati da sallama da duniya, ko motsin kirki batayi, dan da kyar take iya jan numfashi ma. ...Shikuwa macijin nan ganin bata ko motsine yasa ya sauƙo daga ruwan cikinta ya tsaya saitin fuskar ta tare da fasa kansa yana huci, matsowa yayi sosai jikin fuskar tata yana hura mata iska daga bakinsa, sannan ya ɗan ja da baya ya tsaya yana kallon ta. Ahankali fattu ta ɗan buɗe idanunta dan ganin shin me kuma macijin nan ke shiryawa? Ta yaya yake tsara kasheta itama, saidai tana buɗe idanta suka sauka akan na macijin nan ya ƙura mata idanunsa. Cike da tsoro da fargaba fattu ta kafe shi da nata idanun, sai kawai ta ji ta tsinci kanta da kasa daina kallonsa, abubuwan mamaki take gani tare da macijin, sam kwayar idanunsa ba irin ta macizai bace, shi wannan sak! irin ta mutane ce saidai gurin farin yayi wani irin kala kala, blue yellow pink, Amma asalin kwayar baƙiƙirin take. Sai kuma taga hawaye na zubowa daga idanun macijin kamar mutum yana kuka. "Innalillahi wa'inna ilahirin raji'un, Allahumma ajirni fi musibati waaklifni kairan minha, la'ila ha illa anta subhanaka inni kuntu minazzalimin" Shine abinda fattu ta fara karantawa cikin zuciyarta jikinta na wani irin tsuma da karkarwa, tunda take bata taɓa ganin irin wannan macijin ba sai yau, ya maciji zai kasance da idanun mutane? sannan kuma jikinsa akwai banbanci sosai dana macizai, dan shi yana da wani irin jiki mai ban mamaki yadda kalar idanunsa ta kasance haka shima jikinsa yake, sannan kuma bai kai girma irin na macijin jiyan nan ba amma yana da girma shima sosai, kuma dogone na gaske. Kallon kallo kawai ake tsakanin fattu da macijin nan, inda ahankali ya fara hucewa daga kumbura da fasa kan da yayi, Fattu na kallonsa harya koma normal jikinsa ya daidaita, sannan ya fara ƙoƙarin barin ɗakin ta wata yar hanya dake jikin katangar karan, wacce ita fattu sam bama tasan da ita ba sai yau, da alama dai shi yayiwa kansa hanyar. Saida yaje gab da hanyar tasa sai kuma ya juyo da kansa yana kallon fattun, shi bai tafiya ba kuma bai dawo ciki ba. Sosai jikin fattu ke rawa tana zubda hawaye, dan yau kam lamarin ya kulle mata kai, wai wannan wane irin MACIJINE? shin macijin ne ma kokuma wata halittar? sannan maiyasa yaƙi yi mata komai, sai dai ƙoƙarin ceto ta da yake atsammaninsa na ko bata numfashi? haƙiƙa akwai abin dubawa dan gane da wannan macijin. "Fattu ! fattu!! ki tashi ki yi salla lokaci yana ja fa" ta tsinkayo Muryar baffa daga wajen ɗakin yana mata magana . Jin muryar baffa da fattu tayi sai hankalinta ya ɗan kwanta cikin ɗaga murya tace "baffa kazo ka taimaka min gwogwgo bata motsi" ta faɗa cikin Muryar kuka tana kallon macijin. Cikin sauri da azama baffa ya shigo ɗakin yana faɗin "Subhanallah me kuma ya sami Hansai din? Cikin kuka fattu ta kalli baffa sannan ta kalli inda macijin nan yake har lokacin yana tsaye yana kallon ta, "Baffa bansani ba kawai ta shigo tana dukana sainaga ta faɗi ƙasa" abinda fattu ta tsinci kanta kenan da faɗa murya na rawa. Ahankali macijin nan ya juyar da kansa ya bi ta yar ƙofar nan ya fice. Sai lokacin hankali fattu da nutsuwarta suka dawo jikinta, cikin ƙarfin hali ta yunƙura ta tashi zaune, har lokacin akwai alamun tsoro da firgici akan fuskarta, dan jikinta sai rawa yake. "Washhhh hannuna" ta faɗa ahankali tana mai runtse ido, dan sosai hannun ke mata mugun ciwo. Ruwa baffa ya ɗebo mai sanyi wanda ya tara na sama, yana zuwa ya kwarara wa gwogwgo ruwan a jikinta, aikuwa azabure ta tashi zaune tana ihu "wayyo Allah na maciji zai kasheni malam kawo ɗauki, fattu tayimin turen maciji, wayyo wuyana, wayyo hannuna na shiga uku na lalace" abinda gwogwgo hansai ta farka dashi kenan, maimakon ambaton sunan Allah . "Kinga hansai ki nutsu ba wani maciji anan nine bukar wannan kuma fattu ce ɗiyarki" cewar baffa kenan a ƙoƙarin sa na kwantar mata da hankali. Buɗe ido gwogwgo tayi sosai ta kallesu kafin tace "kuturin bala'i Allah ya kiyaye wannan sheɗaniyar ta zama ƴata mayyace fa, wllh ture tayimin yanzun na wani maciji ya kusan hallakani, ai komai zai faru sai dai ya faru amman sainaga bayan yarinyar nan Shegiya may.......wayyo Allah na ya dawo ya dawo Malam" gwogwgo hansai ta faɗa sakamakon hango kan macijin nan da tayi, ai da gudun gaske ta fice daga ɗakin tana ihu . Girgiza kai baffa yayi yana mai Allah wadai da halin matar tasa, shikam yasan sam baiyi dacen mata ba. Kallon Fattu yayi wacce take riƙe da hannunta mai ciwon, hawaye a zaba na zuba a idanunta. "Ashsha ashsha fattu kiyi haƙuri kinji, komai yayi farko zaiyo ƙarshe, Allah yana sane da halin da kike ciki in sha Allahu zakiyi dariya anan gaba" Baffa ya faɗa cikin sanyin murya da ƙoƙarin kwantar mata da hankali. Ahankali ta sanya hannu ta share hawaye idanunta, kafin tace "Baffa hannu na ciwo yake min" ta faɗa tana nuna masa hannun dayake mata ciwon. Kallon hannun yayi yanda ya kumbura yayi suntum dashi, cikin tausaya wa yace "Ayya faɗimatu sannu. Kinji maza daure kiyi sallah saina duba miki hannu kiyi haƙuri, Allah yayi miji albarka" ya faɗa yana mai taimaka mata ta mike tsaye. "Ameen baffa "Ta faɗa tana ficewa daga ɗakin. Bayi ta shiga ta kama ruwa sannan tayi alwala cikin dabara kafin ta fito ta koma ɗakin, Sallah tayi tare da karatun alƙur'ani mai girma, da ka take karatun dan da ahaka aka koya mata, bayan ta idar ne baffa ya shigo ɗakin ɗauke da kwarya ahannunsa. "Sannu Fattu karɓi wannan madarar Kisha kinji, saina duba miki hannun" Baffa ya faɗa yana miƙa mata kwaryar. Bata da zaɓi dan haka ta katɓi kwaryar tare da yin Bismillah ta kafa kanta, saida ta shanye kafin ta ajiye kwaryar . Allah Sarki Fattu tasha wahala sosai lokacin da baffa ke gyara mata hannun, kasancewar yayi tsami sosai, kuka take harda su majina, haka baffa ya gyara mata yana mata sannu. Bayan ya gama gyara mata ne yace ta kwanta ta huta kafin garin ya gama wayewa. Ahaka ta kwanta tana ajiyar zuciya, inda bata jima ba barci yayi awon gaba da ita, abinka da wanda bai sami barci ba dama. Ficewa baffa yayi daga ɗakin ya nufi nashi cike da tausayin ƴar tashi dayake matuƙar ƙauna. Ko minti talatin batayi da fara baccin nan ba ta tsinkayo muryar gwogwgo tana kiranta "Ke gantalalliya mayya fito dan ubanki ,ko uwarki ce zata miki aikin?Shegiyar yarinya aljana wllh bakici bulusba yadda kika sa macijin nan ya lagartamin jiki to wllh saina rama ,fito ki ɗebomin ruwa yanzun nan . Afirgice fattu ta tashi daga barcin ta fito da gudu tazo tana rawar jiki ,Dan bala'in tsoron gwogwgo take kamar ranta."gwogwgo dame zan ɗebo ruwan "ta faɗa kanta asunkuye. Da ubanki zaki ɗebo ruwan kinji ?kije ki nemomin kuɗin da zaki biyani bokatina inyaso ki ɗebomin ruwan aciki"gwogwgo ta faɗa tana daga ɗaki,dan taƙi fitowa waje kartaje macijin nan ko ajikin fattun yake. Har fa a wannan lokacin yaran gwogwgo hansai suna kwance aɗaki suna barci. Amma take ƙoƙarin tura fattu ɗiban ruwa da wannan safiya,alhalin bata da lafiya.dan lokacin da baffa ke gyara mata hannun tana jin ihunta.lokacin tana kwance akan gado tana hucin azabar da macijin nan ya gana mata,"Shegiyar yarinya Gara kemaki ɗandana azabar dana sha ,Allah yasa hannun ya karye ma kowa ya huta. "Dan Allah gwogwgo kiyi haƙuri wllh bansan inda zan samo kuɗin ba kiyimin rai "fattu ta faɗa cikin kuka. "Dan kan ubanki tashi ki ɓacemin da gani,wllh kome zakije kiyi bai dameni ba Indai zaki kawomin murtala uku da raina gomata."ta faɗa tana rarumo wani busasshen kwanon tuwo aɗakin ta cillowa fattu shi. Allah ne ya kare fattu da tuni kwanon ya sauƙa akanta ,tayi saurin ficewa da gudu daga gidan. "Shegiya da kin tsaya ai"cewar gwogwgo tana mai kwanciya ba ko sallar safiya. Koda fattu ta fita daga gidan kuka take sosai ,batasan inda zata nufa ba ,ina zata samo Murtala uku da Naira goma?waye zai bata waɗannan iyayen kuɗin? Kodai gurin jauro zataje tace ya taimaka mata da Murtala uku da Naira goman?kai a'a bazataje ba, dan jauro ba mutumin kirki bane ,ranar nan ma hannunta yake ƙoƙarin kamawa wai yana sonta,kuma baffa yace maiyin hakan ba mutumin kirki bane. Kusan minti biyar tana saƙa da warwara,kafin ta yanke shawarar kawai ta tafi bakin rafin ta zauna ko Allah zai sa ta sami abun ɗiban ruwan. Tafiya take ahankali ,wanda kallo ɗaya zaka mata kasan batajin daɗi,hannunta mai ciwon kuwa ta rikeshi da ɗayan hannun.haka ta nufi rafin dake can bayan gari cikin jeji. "Hai jauro wai kuwa kaga Abinda nake gani"? Cewar haroji kenan wanda suke zaune akan wata bishiya shida jauro can kusa da rafin da fattu ta nufa. "Wanda aka kira da jauron ne ya ɗago kanshi dake duƙe yana zuƙar sigari yace "me ka gano mana"? "Wllh fattu ce kuma ita kaɗai kaganta can ta nufi rafi"ya faɗa cikin ɗoki da zumuɗi. Da sauri jauro ya kalli gurin da harojin ke nuna masa ,aikuwa fattu ya hango ,cikin hanzari ya fito daga kan bishiyar yace "wayyeee huuhuuu ,yau kam mun fito asa'a dan wllh saimun aikata mata ,wllh saina kusan cinye fattu yau "ya faɗa cikin murna da farin ciki yana mai bin hanyar da fattu ke tafiya,harta kusan ƙarasawa rafin. Da sauri haroji yabiyo bayansa yana faɗin"ai wllh nima saina ɗana yau ɗinnan inka gama saika birmin siɗi" Da sauri suke tafiya dan haka cikin ƙanƙanin lokaci suka cimma ta.kawai sai gani tayi sun sata atsakiya. Kallonsu tayi cikin tsoro da fargaba,tace"meye hakan jauro ku bani hanya in wuce"ta faɗa cikin dakiya da nuna alamun bata tsoro su. Dariya suka kyalkyale da ita ,kafin jauro yace "wllh fattu yau saina kusan shinyeki gaba ɗayanki Allah ne ya kawo mana ke dan haka maza kwanta "ya faɗa cikin jahilci da rashin imani. Cikin tsoro da fargaba fattu ta fara ja baya tace"jauro me na maka zaka cinyeni?dan Allah kayi haƙuri wllh bana son mutuwa yanzu ina son ganin innarta"ta faɗa lokacin harta fara zubar da hawaye. Dariya suka saka sakawa suna tafa hannu kafin haroji yace"jauro kawai kamata da shegen ƙarfi dan bazata kwanta ba ,kuma fa kamar bata san me kake nufi ba " aikuwa jin haka sai jauro ya cakumo fattu yana faɗin aikuwa yanzu zata san me nake nufi ,yarinya kin cika kin batse amma ba mai amfana dake" nan da nan suka fara kokawa,yana ƙoƙarin Kaita ƙasa ,ita kuma tana Turkewa da ƙoƙarin kwatar kanta. kasancewarsa namiji tuni yaci ƙarfinta dan har ya Kaita ƙasa,ga ciwon hannu. Daram ya zauna akan ruwan cikinta yana ƙoƙarin cire mata riga.dan tuni shikan ya cire wandonsa daga shi sai wata yar Shara ajikinsa banda wari ba abinda yake yi .haroji kuwa yana tsaye ya juya baya yana gane musu koda me tahowa. Ihu fattu take cikin tsantsar tsoro da tashin hankali ,tayi mugun razana da ganin abinda jauro ke ƙoƙarin tura mata a bakinta yana fadin"maza Kisha fattu haka ake mana lagus sha maza kiji akwai daɗi"ya faɗa yana ƙoƙarin tura mata jauronsa abakinta wacce ganinta kaɗai ya mugun tsorata fattu.dan bata taɓa ganin wannan ƙaton abun mai numfashi haka ba sai yau. "Wayyo Allah na shiga uku jauro menene wannan kake ƙoƙarin bani abakina ka bari bana so wayyo hannuna ,wayyo baffa zan mutu" ta faɗa tana wani irin kakkafewa jikinta na wani irin ɓari. "Wllh yau ko zaki mutu fattu saina kusan cinyeki dan na jima da yunwarki araina, yau kuwa ba mai hanani yin.......wayyo Allah menene wannan haroji maza zoka taimakeni"jauro ya faɗa lokacin da yaji wani gibgegen abu ya fado kansa ya duƙunƙune shi sannan yasa baki ya cafke aliyarsa. _Ihu jauro ya kurma mai ƙarfin gaske ya faɗi can gefe yana burbura tare da rikan "wayyo haroji jaurota zai cinyemin ka taimakeni zan mutu wayyo maciji "ya ƙarasa faɗa da kyar sakamakon wata danƙa mai ƙarfi da macijin nan yayiwa jauronsa har saida numfashinsa ya ɗauke . Haroji kuwa ya mugun tsorata ganin halin da jauro ke ciki,ga wannan ƙaton macijin daya kanannadeshi yana ƙoƙarin karya masa ƙasusuwa. Cikin kiɗima ya rarumo wani ƙaton dutse yayi kan jauro da wannan macijin,yana zuwa baiyi wata wata ba ya ɗaga dutsen ya kwaɗawa macijin nan abayansa. Aikuwa nan da nan bayan macijin ya fashe jini yayi tsartuwa har kan fuskar haroji,wani ihu haroji ya kwala ,sakamakon sauƙar jinin macijin nan akan fuskarsa ji yayi kamar an watsa masa ruwan batir,nan da nan gurin ya sale kamar wanda ya ƙone sai turiri gurin yake. Jifa haroji yayi da dutsen hannunsa yana ihu yana faɗin"wayyo Allah idona bana gani wayyo kwayar idona ta zazzage na shiga ukuna "abinda yake daɗi kenan yana ihu da tsalle. Shikuwa macijin nan silalewa yayi daga jikin jauro ya koma gefe guda tare da kwantar da kansa akasa ,dan kuwa sosai haroji ya kwada masa dutsen nan,kuma da alama ya shige shi . Gaba ɗayan abinda ke faruwa akan idanun fattu ,tana kwance tana kallon ikon Allah,tabbas zuwa yanzu ta gama yarda cewa macijin nan bashi da biyar cutar da ita ,saima taimakon ta da yake,shin wanene wanan macijin?meye alaƙarta da shi?me yake nema agurinta?anya ma MACIJINE wannan ?kodai aljanine yake zuwa mata asiffar macijin? Wadanna sune tarin tambayoyin da fattu ke yiwa kanta tana daga kwancen wanda bata da amsarsu. Saidai kuma gaba ɗaya hankalinta ya tashi ganin yadda macijin nan ya kwanta lamo kamar ya mutu.nan da nan tsoro ya mamaye zuciyarta ,cikin dauriya da jarumta ta yunƙura ta miƙe tsaye tana yamutse fuska,hannunta mai ciwon yana riƙe aɗaya mai lafiyar. Gurin macijin ta nufa gabanta na ci gaba da faɗuwa,dan tsoro take kar ita kuma yayi mata wani abu.tana ƙara sawa ta durƙusa ahankali dai dai inda haroji ya buga masa wannan dutsen ,hannu ta sanya ahankali ,cikin karkarwa jiki ta ɗan shafa gurin ciwon.ai tana ɗora hannunta agurin macijin nan yayi wata irin juyowa tare da fasa kai kamar zai sareta, cikin tsoro da fargaba ta cire hannunta tare da matsawa baya da sauri tana zare ido tana kallon macijin. Shima yana juyowa yaga fattu ce ,sai ya tsaya yana kallon ta,tare da komawa yadda yake ,wato ya sassauta fusatar da yayi ,kawai ya tsaya yana kallon ta. Itama kallonsa take cikin tsoro da bugawar zuciya,ahankali macijin ya fara tahowa ,har ya zo gareta ,runtse idanu tayi tana karanta addu'ar Allah ya tsareta. Ga mamakinta kawai saitaji macijin ya hau kan cinyarta ya kanannaɗe jikinsa ya dora kansa a saman gammon da yayi da jikinsa. Ahankali ta buɗe idanunta tana kallonsa,shima ita yake kallo saidai idanunsa na zubar da hawaye kuma na jini . Jikinta kawai rawa yake cike take da tsantsar tsoron abinda zai faru .juyawa tayi tana kallon haroji dake ta faman ihu yana yaɗuwa kasa.sannan ta kalli jauro wanda yake kwance ba alamun numfashi atare dashi,ga jauronsa nan tayi wani irin kumbura na ban mamaki sai jini ke zuba . Tsorone ya ƙara kamata cikin azama ta yunƙura tare da mikewa tsaye, ture macijin tayi daga jikinta ta kwasa da gudu tayi gida tana kuka . Koda taje gidan, da sanɗa tayi saurin shiga ɗakinta tana kuka,zama tayi akan tabarmarta tare da kife kanta a tsakanin cinyoyinta tana kuka.damuwace fal cikin ranta,wai meke shirin faruwa ne da rayuwarta?wacece mahaifiyarta?waye wannan macijin da yake ɗaukan hukunci akan duk wanda yayi nufin cutar da ita?tanasan sanin wannan macijin waye shi,kokuma waye ya aikoshi gareta.tana cikin kukanta ne kawai taji abu yana hawa jikinta silililili!!! Afirgice ta ɗago kanta tana kallon macijin daya gama hawa jikin nata. kansa ya ɗora akan wuyanta yana fidda wani irin huci ,shiru tayi tana sauraron yadda macijin ke huci,sanan jikinsa yayi wani irin zafi sosai.duk yadda akayi bashi da lafiya ,kuma dukan da haroji yayi masane solar hakan. Tausayinsane taji yayi mugun kamata,ahankali cikin tsoro ta miƙa hannunta tare da riƙo saitin wuyansa ahankali ta janyoshi, ko motsi baiyi ba bare ya hanata abinda yake yi ɗin. Akan tabarmar ta ɗorashi tare da ci gaba da kallonsa,cikin muryar kuka tace "bawan Allah kai waye?meke tafe dakai?waya aikoka zuwa gareni?meyasa kake ƙoƙarin daukar mataki akan duk wanda ya zalumceni?dan Allah karka cutar dani, bani da kowa sai baffana,dan Allah kayi tafiyarki ,idan mutanen garin na suka farga da kai zasu kasheka ,bazan so hakan ba dan Allah na roƙeka ka tafi"ta ƙarasa maganar tana haɗa hannunta cikin kuka. Shidai macijin nan ko motsi baiyi ba sai huci da yake yi sosai, Ahankali ta kalli gurin da yaji ciwo dazu sai taga gurin yana turiri kuma yayi wani fari fat.shiru tayi tana kallonshi ,yanzu ya zata yi masa ne?dan da alama fa yana jin jikine, data rasa abinyi kawai saita lulluba zanin sallarta ta fara karatun Alqur'ani mai girma.cikin abinda bai wuce sakwan biyar da fara karatunta ba kawai macijin nan ya fara wata irin murmurɗewa yana sauya kala, da farko yayi jajur dashi,sai kuma yazo yayi baƙiƙirin sosai ,wani irin hayaƙi na fita daga jikinsa . Duk abinda yake sam fattu bata kulaba ,dan ta ɗaga kanta sama ne tana karatun ,kuma idanunta na zubda kwalla. Shikuwa macijin nan burburwa ya ci gaba dayi yana murɗewa jikinsa na turiri tare da sauya kala.can kuma ya fara wani irin ƙara mai kama da gurnanin zaki.cikin tsoro fattu ta dawo da kanta ƙasa tana kallon macijin , sakamakon wannan sautin ƙara da taji yanayi.sai lokacin hankalinta ya kai kanshi taga abinda ke faruwa. Tsorone ya kamata ƙarara "innalillahi wa'inna ilaihir raji'un"shikenan ta tabbata wannan ba maciji bane tabbas aljanine ,ko kuma aljanine ya shiga jiki sa,na shiga uku ni fattu ya zanyi da rayuwata?meke shirin faruwa dani" ta faɗa cikin muryar tsoro da shiga ruɗu. M4 Shikuwa macijin nan tana daina karatun saiya daina burburwar da wanann gurnanin,ahankali kuma jikinsa ya dawo yadda yake . Ya jima kwance lamo kafin ya fara motsi,kansa ya ɗago tare da fasa kan yana kallon fattu,gaba ɗaya idanunsa sun koma baƙiƙirin dasu sannan wasu irin ƙananan layoyi suka bayyana kusan guda uku aƙasan kanshi, sai wani irin motsi suke kamar ya'yan tsutsa. Karkarwa jikin fattu keyi kamar an saka mata shokin, lamarin ya matukar bata tsoro ,meye wannan ɗin haka suka bayyana jikin macijin nan? Me yasa daga fara karatun Alqur'ani gaba daya ya sauya kama?tabbas akwai wani boyayyen al'amari game da wannan halittar dake gabanta,kuma zata ci gaba da bibiyar macijin nan sannu kan hankali har saita gano menene tattare dashi. Tana nan maƙale jikin katangar karan kamar ƙadangaruwa dan tsabar tsoro da shiga shock ,idanunta ƙuri akan macijin ,wanda shima ita yake kallo ,kusan minti biyar suna haka ,taga macijin ya sulale ya bar ɗakin ta wannan hanyar tashi. Rarraba idanu ta farayi tana dafe da ƙirjinta ,yau kam tana ganin ikon Allah kala kala ,anya kuwa bata janyowa kanta masifa ba?waima meye alaƙarta da wannan halittar ne?ko dai baffanta zata sanarwa halin da ake ciki ne?kai a'a ba yanzu ba tukunna ,ya kamata ta zama jaruma tayi wanann aikin koba komai zata taimaki rayuwar macijin,dan ta fahimci akwai boyayyen al'amari atareda shi. Haroji kuwa gaba ɗaya ya fice daga hayyacinsa sai ihu yake yana faɗuwa ƙasa ,ahaka ya nufi gidan lamiɗon garin ,wanda shine mahaifin jauro ,yana ihu yana tumami, har yaje gaban lamiɗo ya faɗi yana "wayyo idanuna ,wayyo fuskata lamiɗo ka taimaka min. Ruɗewa lamiɗo yayi wanda yake tsaye jikin wata sanuwa yana bata ciyawa, lamiɗo bashi da imani ,azalumine sosai ,kuma mutanen garin suna matuƙar tsoronsa, dan haka yake mulki na zalumci agarina,ganin halinda haroji yake ciki ya sashi tsayawa cak da abinda ke yi ya dube shi yace "Kai haroji menene hakan ?ina jauro?me yasameka? Waɗannan sune tambayoyin da lamiɗo ya dinga jerowa haroji wata na bin wata. Cikin azabar ciwo da fitar hankali haroji yace "jauro ya mutu maciji ya cinye masa jauronsa yana bakin rafi" Ai dajin wannan batu hankalin lamiɗo ya tashi ,nan da nan yayi kan haroji yana faɗin wane macijin ?me kake cewa ?jauro ya mutu?ƙaryane badai agarina ba ,ba wanda ya isa ya zo garina ya kashe min ɗana."lamiɗo na gama faɗin haka ya kira mazan garin ,ya sanar dasu maza aje bakin rafi ataho da jauro. Aikuwa cikin ƙanƙanin lokaci aka ɗauko shi kamar gawa . Nan da nan lamiɗo ya nemi haroji ya sanar dasu abinda ya faru . Nan ya sanar dasu iya abinda idanunsa suka gani,dan shima yana cikin mugun halin mutuwa ko rayuwa dan tuni gurin da jinin nan na macijin ya taɓa ajikinsa yayi wani irin kore shar yana zubar da wani yallow ɗin ruwa . "Lamiɗo fattu ce ta Turo mana macijin nan ,shine ya kashe jauro"abinda haroji ya faɗa kenan ya sume. Nan da nan mutanen gurin suka fara maganganu Suna faɗin da "Dama hansai ta faɗa tace mayyace yarinyar ,tunda har ta fara kashe mutane ba zasu yarda ba sai an hukunta itama. Ran lamiɗo ya ɓaci sosai ,dan dama yana jin haushi yarinyar da ubanta,ya shirya neman aurenta amma sam taƙi yarda wai karatu take,yanzu kuwa dama tasameshi da zai hukunta su ita da tsohon nata.dan haka cikin bada umarni yace lallai lallai aje ataho da fattu da ubanta . _____Nan da nan fusatattun rugar suka nufi gidan malam bukar ,dan aiwatar da ƙudirin lamiɗo. Allah Sarki fattu kuwa a wanann lokacin tana ɗakinta cikin jimami da tunanin abinda ta gani yau ɗin nan,haka nan ta tsinci kanta da son sanin menene wannan abubuwan dake motsi aƙasan wuyan maciji? wanda tun daɗewa bata taɓa ganinsu ba sai yau,waya sani ma ko wani akayiwa asiri ajikin macijin ?tabbas zatayi iya ƙoƙarin ta dan ganin ta raba macijin nan da wannan abubuwan ,ta yadda koda wani aka yiwa asiri ta hanyar macijin, to asirin zai karye .sannan tana fargabar gwogwgo ta gano cewar tana gidan kuma bata ɗebo ruwan ba.kuma ahalin da ake ciki yanzu bazata iya komawa rafin nan ba ,.dan ta tsorata dasu jauro . Hayaniyar mutane ce ta cika gidan nasu fattu ,wanda haka yasa gwogwgo hansai fitowa dole badan ta soba, Dan har lokacin nan ita da yaranta ba wanda yayi sallar asuba. "Kai su waye haka suka zo suka cika mana gida da ihu kamar ana yaƙi?"cewar gwogwgo hansai tana gyara daurin ƙirjinta dake ƙoƙarin kuncewa bayan ta fito daga ɗakin. "Aa meye hakan arɗo ?lafiya na Ganku da yawanku kun shigo?ta tambaya lokacin da idanunta ya sauka akan mutanen da suka cika gidan,kusan duk mazan garin ne. Cikin masifa wanda aka kira da arɗo yace "wllh yau saimun ɗauki mataki akan bukar da fattu ,haka kawai yarinya ta fara kashe mutane ,kuma ta rasa ta kan wa zata fara sai ɗan gidan lamiɗo ?wllh yau sai mun kashe Shegiyar yarinyar nan"ya faɗa yana wani zazzaro idanu kamar zararre. Eh wllh afito mana da ita kawai mukaita gurin lamiɗo ya bamu izini mu kashe mayya.gaba ɗayan matasan dake bayan Arɗo suka haɗa baki wajen faɗi haka cikin nuna fusata da ƙosawa abasu fattun . Wani irin farin ciki da jin daɗine ya kama gwogwgo hansai ,shikenan zata rabu da alaƙaƙai cikin sauƙi Allah yasa akasheta kowa ya huta ,dama su haɗa da bukar ɗin da yake ɗaurewa fattu gindi ,koba komai shanunsa sun zama nata.gwogwgo hansai ta faɗa cikin ranta.kafin ta kalli arɗo da sauran mutanen tace "aikuwa idan aka kasheta an kyauta ,dan nima nan wllh so take ta cinyeni nida yarana, jiya da kyar mukasha data maƙuremin wuya wai saita cinyeni, ku ɗan jira kaɗan yanzu zaku ganta shegiya gantalalliya,banma san inda ta tafiba, dama haka takeyi kullum inta fice yawon iskanci bata dawowa da wuri,tana can gurin maza"gwogwgo hansai ta ƙarasa maganarta tana mai buga hannu acinyarta. "Aikuwa yanzu zamuje mu nemota ko ina ta shiga, ina mu kasu gida 3 wasu sutafi bakin rafin wasu sushiga jeji, mukuma zamu jira ana "cewar arɗo kenan yana kafe sandarsa akasa,sannan ya gyara tsayuwarsa. Duk wannan abunda ke faruwa akan kunnen fattu, tana jin komai ,saidai tashin hankali,firgici tsoro da kuma ruɗewa sun hanata koda yin kwakwkwaran motsine . Numfashinta ma da ƙyar yake fita tsabar ruɗewa. Ta shiga uku !shikenan yanzu kasheta za'ayi?laifin me tayi da za'a kasheta?me baffanta yayi ake nemansa shima? Dama jauron mutuwa yayi ? innalillahi !!!yanzu ya zatayi. Wani kukane ya kubce mata cikin sauri ta toshe bakinta tana kuka sosai kamar ranta zai fita,ji take dama tana da ikon ɓacewa, tabbas da ba abinda zai hanata ɓacewa ta bar duniyar ma gaba ɗaya. Ahankali ta miƙe cikin sanɗa ta leƙo da kanta ,ba ƙaramin tsoro tajiba lokacin da taga mutanen da suka zo tafiya da ita.shikena kawai ta mutu,yanzu shikenan bazata cika burinta na ganin innarta ba?wayyo "Allah ka kawomin ɗauki "ta faɗa cikin raunananiyar muryarta mai cike da tsantsar tsoro. Ahankali ta ƙara leƙo da kanta waje ,cikin rashin Sa'a kuwa sukayi ido huɗu da dan gidan gwogwgo hansai umaru.wanda hayaniyar mutane tasa suma suka farka. "Laaaah Ardo, gwogwgo ga fattun can cikin ɗakinta tana leƙowa"ya faɗa yana nuna ɗakin da Fattu ke ciki. Cikin hanzari fattu ta koma cikin ɗakin tana mai runtse idonta tare da dafe ƙirjinta. "Shikenan sun ganni wayyo Allah na baffa,wayyo MACIJINA kana ina kazo ka taimakeni zasu kasheni wayyo ni fattu" Fattun ta faɗa tana mai leƙa hanyar nan da macijin Kebi idan zai bar ɗakin nata inya zo, kamar zararriya haka Fattun ke bankada hanyar macijin da hannunta. "Munafuka mayya dama kina ji ana neman ki shine kika ɓuya nan? To fito yau dubunki ta cika, mutuwa zaki yi wllh sai kin bar duniyar nan yau nima na huta da ganinki, maza arɗo zoka tafi ta ita gata nan"gwogwgo hansai ke faɗin wannan maganar tana daga bakin ƙofar dakin Fattu, dan tun lokacin nan da tasha matsa agurin maciji bata ƙara shiga ɗakin Fattun ba. Aikuwa kafin ta rufe baki su arɗo sukayo kan Fattu suna janta. "Wayyo Allah gwogwgo karki bari su tafi dani zasu kasheni ,wllh ban aikata komai ba wayyo Allah na gwogwgo ki taimaka min"abinda Fattu ke faɗi kenan tana miƙawa gwogwgo hannu cikin kuka mai tsanani. "Ai wllh dana taimakeki gara hannuna ya karye Shegiyar yarinya ,kutafi da ita can ku kashe banza" gwogwgo ta faɗa tana kaɗa hannu irin yadda ake korar kaji ,cikin farin ciki take maganar. Ihu Fattu keyi tana kuka,amma haka suke janta kamar akuya aƙasa, suna cikin tafiyar ne sai ga baffa aguje yazo gabansu sai kuma suka tsaya, shima Baffa tsayawar yayi yana riƙe da sanda sai haki yake, dan yana can bayan gari ya sami labarin abinda ke faruwa acikin garin da gidansa, shine ya rugo yazo . Aikuwa Fattu na ganin baffa ta ƙara fasa ihu tana cewa" wayyo baffana ka taimakeni zasu kasheni" ta faɗa tana miƙa masa hannu, abin tausayi dukta susuce tayi buju buju da jiƙaƙkiyar ƙasa.kallonta baffa yayi Cikin bacin rai mai tsanani ya ce. "Sakarmin yarinya arɗo kona rotsa maka sandar nan akanka" baffa ya faɗa cikin hargowa da ƙaraji. Kasancewar baffa kowa ya sanshi arugar mutumin kirki ne sam ba ruwansa da shiga harkar wani, sannan kuma shine ke ja musu jam'i ,hakan yasa suke ɗan ganin girma da mutuncinsa, dan haka cikin Turo baki da hura hanci arɗo yasaki hannun Fattu wanda ke mata azabar ciwo da raɗaɗi, yana mai cewa" ato lamiɗo ne dai yace mu taho daku, dan haka ya zama dole ayiwa lamiɗo biyayya"ya faɗa yana hararar gefensa, dan yaji haushin sakin wannan hannun na Fattu mai shegen laushi da daɗin taɓawa da Baffa yasa yayi. Fattu kuwa yana sakar mata hannu ,da rarrafe ta ƙara so gurin baffa ta rirriƙe shi tana kuka da faɗin" wallahi baffa ba abinda na aikata ban kashe jauro ba" ta faɗa cikin matsanancin kuka da tsoro, jikin ta sai rawa yake. Riƙota baffa yayi cikin tausayawa yace "na sani Fattuna baki kashe jauro ba, kuma ba wanda zai kasheki, Allah na tare dake kinji" Ya faɗa cikin sigar rarashi, sannan ya kalli arɗo yace "kai arɗo ka kiyayeni, karka ƙara ƙoƙarin sake aikata irin wannan dabbacin akan ƴata, saboda baka da hankali shine zaka rinƙa janta aƙasa kamar wata dabba ? Jahilan banza jahilin hofi, muje gurin mai garin zanji idan shiyasaka wannan ɗanyen aikin" baffa ya faɗa cikin mugun bacin rai yana mai riƙe Fattu suka nufi faɗa. _Kai tsaye su baffa suka nufi gurin lamiɗo, hannunsa riƙe da na fattu wacce ke tafiya ahankali cikin azabar raɗaɗin da hannunta keyi ga kuma ciwon jiki. Yayinda su arɗo ke mara musu baya burinsu kawai suga wane irin hukunci lamiɗo zai ɗauka akansu fattu, cikin zuciyar arɗo yake fatan inama lamiɗo ya kori su fattu daga rugar, inyaso su bisu hanya suyiwa fattun fyaɗe, dan su kashe ƙishirwarta dake cin ransu. Shikuwa mai gari tun daga nesa ya hango su fattu, sai gaba ɗaya nutsuwarsa ta bar jikinsa, ƙuri yayi mata da ido yana haɗiyar yawu da lasar leɓe tamkar tsohon maye. Kallonta yake yana ji kamar yaje ya kamota yayi ɗaka da ita. Haba malam yarinya tayi bul-bul da ita kamar nunannen tumatur, lallai yau zai sha shagali, lamiɗo ya faɗa cikin ransa yana mai kallon fattun. Baffa kuwa suna ƙarasowa gaban mai gari ya nemi guri ya zauna tare da zaunar da fattu kusa dashi wacce gaba ɗaya arikice take, tsorone ƙarara shinfiɗe akan fuskarta, tayi luƙus ajikin baffanta jikinta sai rawa yake, ta kasa ɗaga kanta ta kalli kowa, sai hawaye kawai da take sharewa. Kowa yanemi guri ya zauna, masu tsayuwa suka tsaya, da ƙyar lamiɗo ya iya saita kansa ya aro nutsuwa ya yaɓa akansa, tare da ɓata ransa ya kalli baffa yace "Malam bukar kana sane da irin abinda ƴarka take aikatawa awannan garin? lamiɗo ya faɗa cikin kakkausar murya . Ahankali baffa ya gyara zama kafin yace, naji anata wai wai agari cewar ƴata tayiwa su jauro turen maciji, amma sam ban yarda da wannan magana ba, dan kuwa ƴata ba mai kashe mutane bace, sannan ba mayya bace kamar yadda ake faɗa" Baffa ya faɗa cikin ɗaure fuska . Cike da ɓaci rai lamiɗo ya fara magana. "To wallahi Malam bukar bazan ɗauki wannan abun agarina ba, yanzu ace abun nata ya wuce kan kowa sai kan ɗana? sannan kuma kace wai baka yarda da zancen ba? kana nufin nayi maka ƙarya ne? to bari kaji dole ne saina ɗauki mataki mai ƙarfi akanka da ƴar taka, dan ka nuna rashin ɗa'a a gaban fada. Bayan kuma kowa yaga abinda ƴarka tayiwa yaranmu, dan haka bazan yanke hukunci yanzuba sai zuwa gobe idan yaranmu sun sami lafiya, saboda haka yanzu za'a shiga da ita cikin gida anan zata zauna cikin wancan bukkar da ake ajiye masu laifi . Dan haka kowa ya watse sai zuwa gobe da la'asar adawo nan dan jin hukuncin da zan yanke" Mai gari yana gama faɗin haka ya jingina da jikin kujerar da yake zaune akai. gaba ɗayan mutanen dake gurin sunyi na'am da wannan hukuncin nacewar fattu ta zauna a gidan mai gari, dan karta gudu. Kuka sosai fattu ta sanya tana riƙe hannun baffa "wayyo Allah na baffa ka taimakeni,dan Allah karka bari akulleni adakin hukunci ,wllh bani nayi musu haka ba ,kuma sunzone da nufin keta min haddi baffa ka kalli Yadda ya famamin targaɗe na wllh ba laifi na bane" fattu ta faɗa cikin matsanancin kuka kamar zata shiɗe. Cikin tashin hankali baffa ya riƙe hannun Fattu ,ji yake kamar ya fasa ihu,aduniya ba abinda ya tsana irin yaga Fattu cikin damuwa,"kiyi haƙuri fattu ba abinda zai sameki,in Sha Allahu Allah zai saka mana dan wannan mugunta ce ake son yi mana ,kuma Allah yana bayan mai gaskiya"yana gama faɗin haka ya juya gurin mai gari yace "lamiɗo ina neman alfarmar abarmin fattu mu tafi gida ,zamu dawo da ita zuwa goben,dan bata da lafiya kuma barinta ita kaɗai akwai matsala" ya faɗa cikin damuwa da alhinin wannan rashin adalci da ake ƙoƙarin aiwatar musu. Cike da mugunta lamiɗo yace "kai bukar ina ganin girmanka karkasa in daina gani ka iya bakinka a faɗa kake,kasan idan na riga yanke hukunci ba mai ja dani ,dan haka ka tashi ka bani guri tun kafin raina ya gama ɓaci kuma yanzu zansa aje anemomin macijin duk inda ya shiga daga nan zuwa safiya ,"lamiɗo ya faɗa yana mai kiran wasu matasa yace su shigar da fattu cikin bukkar. Kuka fattu keyi tana faɗin"wayyo baffana wayyo Allah ka taimakamin zasu tafi dani wayyo Baffa na karka bari su nemo shi zasu kasheshi. "amma haka suka tura ƙeyarta suka tafi da ita ɗakin hukunci.baffa yana ji yana gani ,hawayene masu zafi suka silalo daga idon bawan Allah ,zuciyarsa kamar ta faso ƙirjinsa yakeji, ashe ma ƙoƙarin keta masa haddin ƴa akayi?amma saboda rashin imani da adalci aka ɗora mata sharri,ba komai Allah zai saka musu. Juyawa yayi ya nufi gida ransa amatukar jagule,yanzu idan wani abun ya sami yarinyar fa?idan wasu suka ƙara yunƙurin cutar da rayuwarta fa?"ya Allah ka karemin yarinyar nan Allah ka duba matsalolin dake kanta da wanda suke shirin samunta.ya Allah ka sauƙaƙa mata ƙalubalen dake gabanta.haka yayi ta mata addu'a harya ƙarasa gida kwata kwata hankalinsa baya jikinsa. Yana shiga gidan gwogwgo hansai ta sanya dariya cike da mugunta harda riƙe ciki tana nuna baffa da hannu."wllh malam Gara ka cire wannan yarinyar daga zuciyarka, inba haka ba kana tsaye zaka yanke jiki ka faɗi ka mutu.ba ruwa na bani da asara, ai wllh banso lamiɗo ya kyaleta wai har sai gobe ba,daya sani yasa anyanke mata kai yau -yau ɗin nan ,da mun huta da nauyinta akanmu" ta faɗa tana turo wani baƙin ɗan kwalinta mai shegen datti zuwa gaban goshinta. Kallon ta kawai baffa keyi ,cikin zuciyarsa yake kissima iri saɓawa gwogwgo da zaiyi dan yau zai nuna mata matsayin fattu azuciyarsa ,sai dai yana yunƙurowa da nufin maida mata martani,kawai yaji bakinsa yayi nauyi,wani irin shayinta da tsoro ya mamaye zuciyarsa.kai kawai ya girgiza ya wuce ɗakinsa ,wato itama gidan mai garin taje kenan?ba komai akwai Allah. Fattu kuwa tunda aka turata cikin ɗakin nan banda kuka ba abinda takeyi, ita damuwarta ma yanzu bai wuce na rashin ganin macijinta ba,duk wannan abunda ke faruwa baizo ba.anya kuwa lafiya?kodai wani abu ya sameshi ne? "Ya Allah ka kare wannan bawan naka ,ka bashi kariya daga sharrin mugayen mutane . Shikuwa maciji adaidai wannan lokacin yana gidansu fattu yaje nemanta bai ganta ba yayi ta zagaye aɗakinta amma bata nan,tun lokacin datayi masa karatun nan daya fita yaje can jeji ya kwanta ,sam bayajin daɗin jikinsa sosai yake jin ciwo ta ko'ina ajikinsa,sai da lokaci yaja sannan ya nufi gidansu fattu ,ahankali yake tafiya cikin ciyawa da jikin katanga, harya ƙarasa gidansu fattu. Koda yaje yaga bata nan saiya yi ta zagaye ɗakin yana nemanta ,amma bata nan. Kwanciya yayi akan ɗaurin kayanta yayi lamo kamar ya mutu.saidai hawayene ke zuba cikin idanunsa . Can kuwa gidan mai gari ,da misalin ƙarfe bakwai na dare sosai hadari ya haɗu agarin, dan haka kowa ya shige cikin gida dan gudun zubowar ruwan da akowane lokaci yana iya sauƙa. Daidai wannan lokacin kuma fattu na duƙunƙune cikin ɗakin hukunci sai kuka take zuciyarta tayi mata ƙunci ga yunwa dake addabar ta rabo ta da abinci tun madarar da baffa ya bata da safe ga kuma hannunta sai zagi yake mata. Ahankali taji ana turo kofar ɗakin hukuncin,da alama shigowa za'ayi,ga duhu aɗakin. Zabura tayi cikin sauri ta miƙe tsaye jikinta na karkarwa,kar dai ace su jaurone suka dawo ?wayyo Allah na " ta faɗa tana dafe ƙirjinta ,zuciyarta kamar zata fito dan tsoro da firgici. Cikin rawar murya tace "wa...w....ayee." Ahankali cikin murya mai kama da raɗa,yace "ke kwantar da hankalinki,nine nan lamiɗo" Ya faɗa yana mai haska tocilan ɗinsa . Cikin zubar da hawaye tace "dan Allah lamiɗo ka fitar dani daga gurin nan ,wllh ban aikata komai ba,bani na kashe jauro ba"ta faɗa cikin kuka. "Kinga ki nutsu jauro bai mutu ba yana raye ,kuma idan kika bani haɗin kai muka yi komai cikin sirri ,to zan kyale ki ki tafi gida abinki"lamiɗo ya faɗa yana matsowa gareta. Ja tayi da baya cikin sauri tace "me kake so nayi maka ?dan Allah ka gyaleni na tafi gida an fara ruwa"ta faɗa cikin kuka,dan ta gano manufarsa ,irin tasu jauro ce ,wato fyaɗe yake son yi mata. Matsowa lamiɗo yayi tare da ruƙo hannunta yana mai cewa"Ayya fattu yarinya mai kyau da kyan jiki ki yarda dani mana duka -duka minti nawa ne ba dayawa zanyi ba kinji ki taimaka min"ya faɗa yana mai janyota jikinsa sosai . "Wayyo Allah na baffa kazo ka taimakeni,dan Allah lamiɗo kayi haƙuri wllh ba kyau kaji tsoron Allah ka tausaya min na roƙeka"fattu ta faɗa cikin rawar jiki da matsanancin kuka,tana mai tureshi daga jikinta,banda warin tsufa ba abinda yake yi. "Ke dan ubanki ki tsaya ko saina miki ta ƙarfine?Shegiyar yarinya haka zamu zuba miki ido muna kallonki kin cika kinyi tunjum dake amma ba mai morarki,ki tsaya dan ubanki"lamiɗo ya faɗa yana mai ɗauke fattu da wani gigitaccen mari Wanda saida ji da ganinta suka tsaya na wucin gadi.kusan minti biyu kafin kwakwalwar ta ta dawo aiki,kuka ta sake fashewa dashi mai tsananin gaske lokacin da lamiɗon ya Kaita ƙasa yana ƙoƙarin dage yar ficiciyar rigar dake jikinta ,wacce jiƙaƙƙiyar ƙasar nan ta gama bushewa . "Innalillahi wa inna ilaihir raji'un wayyo Allah na baffa wayyo mai taimako kana ina?kazo gareni,ina buƙatar taimako ka ahhhhhhhh "fattu ta kwalla wani irin ƙara mai ƙarfi lokacin da lamiɗo yayi......... Tofa masu karatu me lamiɗo yayiwa fattu ne ? Muje zuwa kuci gaba da bin alƙalamin anty mammy. Mrs babi 💘💘 Share and comment fisabilillah More comment More typing. [7/13, 8:11 PM] Aishat Anty: 🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄 MACIJINE🪱🪱🪱 Na mammy kabeer (Anty mammy) Elegant online writers📚📚 Free book Page 13/14 ____________________"Wayyo Allah na Mai taimako kana ina?kazo gareni, ina buƙatar tallafinka, ahhhhhhhhh !!!fattu ta kwalla ƙara mai tsananin ƙarfi lokacin da taji hannun maigari na ƙoƙarin taɓa mata dukiyar fulani ta, tana mai buge hannunsa daga kan ƙirjinta. Ɗaga hannu maigari yayi cikin fushi ya sake ɗauke fattu da wani gigitaccen mari, dan ya fuskanci tana ƙoƙarin kawo masa cikas akan ƙudurinsa, shikuwa ya rantse yau bazai bar wannan damar ta wuce shi ba. "Dan ubanki ki tsaya nayi- nayi abinda ke gabana, wllh yau ko ubankine bukar zai zo gurin nan bai isa ya hanani aiwatar da ƙudirina akanki ba" Mai gari ya faɗa yana ƙara ƙoƙarin maida hannunsa gurin dake tsole masa idanu, wato breast ɗin fattu. Saidai kafin hannunsa ya sauƙa ga inda yake nufin sai kawai yaji wata irin shaƙa da tunda yake arayuwarsa bai taɓa tsintar kansa cikin irin makamancin wannan shaƙar a aduniya ba. Ta ko ina yaji shi aɗaure dam-dam kamar ƙullin buhun goro. Cikin azaba da fizgar magana mai gari yace "wayyo Allah hannuna, na shiga uku wayyo zan mutu" ya faɗa idanunsa azazzare tamkar zasu fito tsabar azaba. Cikin hanzari fattu wacce idanunta ke rufe, ta riga ta gama fitar da rai ta sadaƙar cewa yau shikenan ta rasa budurcinta, dan ta san ba mai zuwa ya ceceta, koda tayi ihu ba mai jin sautin ihunta, sakamakon ruwan saman da ake tsugawa kamar da bakin kwarya. Ba zato ba tsammani tajiyo ihun maigari lokacin da maciji yayi sama dashi ya cilla shi can gefe guda bayan tabbatar da cewa mai gari ya suma, ji kake ƙasss-ƙasss, hannu da ƙafar mai gari na bangaren dama sun karye. Da sauri fattu ta kalli inda akayo jifa da mai gari dan tabbatar da cewar shiɗin ne kokuma yaya, aikuwa cikin wani irin farin ciki da murna ta yunƙura da ƙyar ta zauna tana kuka da dariya,sai kuma ta tafi gareshi cikin rarrafe tana zuwa inda macijin ke tsaye yana huci ya ƙurawa mai gari da ido, da alama yana son ganin maigari ko zaiyi wani motsin ne yaje ya ƙarasashi,duba da yadda yake ta uban huci ya kafe mai garin da ido. Fattu na zuwa ta wani kwaƙume macijin zuwa jikinta ,ta ƙanƙameshi tana kuka kamar ran ta zai fita,kukanta na dalilai biyu ne,dalili na farko shine ganin macijinta na nan araye ba mutuwa yayi ba,kuma masu neman shi basu ganshi ba.na biyu kuma yadda yazo ya kawo mata ɗauki adaidai lokacin da ta fidda rai da cewar zata rasa abu mafi muhimmanci arayuwarta. "Ina ka shiga mai taimakona?na shiga damuwa na rashin ganinka, naji tsoron ko sun kamaka sun kashe ,dan Allah karka ƙara yin nesa dani na tsawon lokaci irin haka,kalli yadda suke son kawar min da budurcina, bansan me na tsare musu ba ,kowa nufinsa ya cutar dani,kai kadai ke sona sai baffana ,bana son na rasa ɗaya daga cikinku, kune rayuwata, farin cikina da jin daɗina,mai taimakona ina sonka har cikin zuciyata, ba ruwana da kasancewarka wata halitta ta daban,Dan kafiyemin halitta irin tawa sau dubu"duk cikin kuka fattu ke faɗin Waɗan nan maganganu,yayi da take ƙanƙame da macijinta kamar zata maida shi cikinta, yadda ta ƙanƙameshi kai kace uwace ake ƙoƙarin rabata da ɗanta. Ahankali macijin nan ke sauƙe wani irin numfashi kamar yana hurawa fattu iska mai sanyi ,da alama dai rarrashinta yakeyi,dan yadda yake huro iskar yana wani rufe ido da buɗewa shine zai fahimtar da kai cewar rarrashinta yake . Zare jikinsa yayi daga ƙwaƙwumar da fattu tayi masa ya zagaye west ɗinta ,Amma Sam bai matseta ba ,sannan ya shigo da kanshi ta ƙirjinta yana kallon fuskarta yadda hawaye yayi faca -faca kan kyakkyawar fuskar tata.kallon -kallo ake tsakanin fattu da macijinta ,kallo yake mata irin na tausayawa. Haƙiƙa abin mamaki ne sosai idan kaga yadda ya wani marairaice fuska yana ƙifta idanunsa tare da ɗan matso da kansa saitin fuskarta,sai kuma ya kwantar da kan nashi saitin da hawayenta ke tsiyaya ta ɓangaren dama, sannan yayiwa ɓangaren hagun ma haka. "Dariya mai haɗe da kuka fattu take yi cike da tsantsar ƙaunar wannan halitta ,hannu ta sanya ta share hawayen daya ƙara zubowa tace "na daina kukan mai taimako tunda baka so ,bazan ƙara ba ka gani ma ko "ta faɗa tana mai ƙara shafe idanunta ,saidai wasu hawayen na ƙara zubowa. Zare jikinsa yayi yana mai hawa kan wuyanta zuwa kanta, saiya leƙo da kansa ta saman kanta ,idan ta ɗago da nufin kallonsa saiya silale ya koma wuyanta ya ɓoye kansa abayanta. Dariya fattu take cikin farin ciki da ganin cewar wai wasa yake mata dan ta sami nutsuwa ta daina kukan ,dan haka lokacin daya ɓoye abayanta sai tace "wayyo ni fattu mai taimakona ya ɓata, ya zanyi da rayuwata ,ina kake abinsona shikenan masu son cutar dani zasu sami dama akaina wayyo ga mai gari nan ya taso"ta faɗa cikin yanayi kamar tana son yin kuka .aikuwa cikin sauri macijin nan ya haye kan cinyarta yana mai fasa kai da wani kalle -kalle ya miƙa kansa can ya dawo dashi can yana huci. Dariya fattu tayi tace "nima ramawa nayi tunda ka boyemin " ta faɗa cikin shagwaɓa kamar wacce ke gaban baffanta ko innarta. Juyowa macijin yayi yana kallonta sai kuma ya ɗora kansa daidai saitin zuciyarta yayi lamo tare da rufe idanunsa.ahankali ta sanya hannu tana shafa kyakyakywan jikinsa mai matuƙar santsi da laushi.kusan minti biyar suna haka,yayinda ake tafaman zuga ruwan sama ,can gefe kuma mai garine shame shame akwance baya motsi.kallon mai gari fattu tayi ,sai taji tsoro ya cika zuciyarta,kodai shima mutuwa yayi, dan ita tama manta da batunsa aɗakin sam,idan kuma ya farka ya ƙara dawo mata fa ,gara fa su gudu daga ɗakin nan tun kafin jama'a su ankare dasu. Cikin muryar tsoro tace "mai taimako ya kamata mu gudu gida karya farka ko wani yazo ya gammu dashi ahaka"ta faɗa tana kallon macijin dake kwance akan ƙirjinta,da alama kuma yana jin daɗin kasancewarsa ahakan. Ahankali ya ɗago kansa tare da silalewa ƙasa yayi hanyar ƙofar fita daga bukkar wacce mai gari ya barta abuɗe tsabar jaraba nacinsa. Binsa fattu tayi da sauri harta fita, saikuma ta dawo ta ɗauke tocilan nan ta mai gari ,dan taga garin yayi baƙi ƙirin kuma har lokacin ruwa ake. Suna fita fattu ta kama sauri -sauri gudu-gudu ,tana tafe tana haska tocilan ɗin nan ,yayinda mai taimako ke biye da ita cikin salon nashi gudun ,saidai suna tafe yana zagayeta ,dan bata kariya ta kowacce kusurwa. Suna zuwa gida kai tsaye fattu ɗakin baffa ta nufa,tana zuwa ta shiga ɗakin ahankali tana haska tocilan ɗin hannunta.Allah sarki baffa yana kan sallaya ya ɗaya hannunsa sama yana ta addu'a,juyowa yayi dan ganin hasken da ake haskowa. "Waye anan"ya faɗa yana kunna tashi tocilan ɗin. Ai da sauri ya miƙe tsaye yayi kan fattu,yana mai cewa"fattu kece alhmdllh fattu na ba abinda ya sameki,?ina mai garin?waye ya fito dake?baffa ya jero mata waɗannan tambayoyin alokaci guda yana mai shafa kanta cikin farin ciki . Ahankali fattu ta kalli gefenta inda macijin nan ke nannaɗe ya fasa kansa yana kallon baffa.tace "baffa wannan ne ya taimakeni, kuma shine macijin daya hukunta su jauro "ta faɗa tana haska macijin da tocilan. Da sauri baffa yaja baya yana faɗin"subhanalla fattu wannan ai MACIJINE ,meye haɗinki dashi,matsa daga gareshi maza karya cutar dake" baffa ya faɗa cikin tsoro yana mai kamo hannun Fattu. "Baffa ka kwantar da hankalinka ,ba abinda zai min ,domin mun jima tare dashi,zauna baffa in baka labarin haɗuwata dashi ,sannan baffa macijin nan yana cikin matsala ,dan da alama anyi amfani dashi wajen yiwa wani asiri. Zama baffa yayi ahankali kan sallarsa ,idonsa akan macijin nan daya matso kusa da fattu wacce ke zaune kusa da baffanta,kallon ikon Allah baffa keyi, yadda macijin nan yayi kane-kane akan cinyar fattunsa ya waniyi lub kamar jariri akan cinyar mahaifiyarsa. Kallon fattu baffa yayi ,yaga ko ajikinta saima hannu data ɗora akan bayan macijin tana shafawa. "Ina jinki fattu faɗa min komai dan hankalinta ya kwanta" Nan fattu ta fara bashi labari tun daga farko har kawo yanzu. Sannan ta ɗora da cewa "baffa dan Allah mu taimaki wannan macijin dan wllh yana cikin matsala ,bakaga yadda ya koma ba lokacin dana ke masa karatu,mu cire masa wannan masifar dake jikinsa"ta faɗa tana nunawa baffa waɗannan layun dake wuyan macijin. Cike da mamaki da al'ajabi baffa ke kallon macijin ,wanda ya ƙara kafewa jikin fattu yana kallon baffa da kuma fattu.baffa yace "haƙika akwai wani ɓoyayyen al'amari dangane da wannan macijin ,kuma in sha Allah zamu taimaka masa iyakar ƙarfin mu tun kafin mai gari ya farfaɗo ya ɗauki matakin kashe macijin nan ,yanzu kije kiyi alwala ki dawo,dan mu fara aiki akansa. Cike da ɗoki fattu ta amsa da" to baffa na ina godiya agareta sosai"sannan ta ajiye macijin gefen baffa tace "mai taimako ai kasan baffana ko?to katsaya agurinsa yan zu zan dawo kaji"ta faɗa cikin murmushi tana shafa bayansa. Kallo ta kawai yayi kafin ya kwantar da kansa ajikin gangar jikinsa dake nannaɗe. Bayan fattu tayi alwala ta dawo dakin ne ta gabatar da sallolin dake kanta ,sannan tayi addu'ar samun nasara akan ceton macijin nan ta shafa.sanna ta juyo gurin baffa wanda ke ta tofa addu'a cikin wata ƙwarya ,zama ta gyara tana mai kallon baffa da jiran ya kammala addu'ar sa. Shikuwa macijin nan yana ganin fattu ta zauna ya silalo ya dawo kan cinyarta ya kwanta,gaba ɗaya jikinsa asanyaye yake,kamar wanda yake tsoron faruwar wani abu.kallonsa fattu tayi tace "mai taimako ba abinda zai sameka ka kwantar da hankalinka ,in Sha Allahu zamu cire maka duk wani sihiri da akayi amfani dakai wajen yinsa"ta faɗa tana mai shafa lallausan san jikinsa mai santsi. Miƙa mata kwaryar nan baffa yayi yace karɓi wannan fattu ki yayyafar masa ajikinsa ,kinayi kina karanta ayatul kursiyyu da falaƙi da nasi, duk abinda zaki gani karki tsorata kinji ?"baffa ya faɗa yana mika mata kwaryar,dan shikam ya gama fahimtar abubuwa da dama aka. Macijin nan. Karɓa fattu tayi cikin nutsuwa ta fara karatun tana kuma shafa masa ruwan rubutun nan ajikinsa. Ikon Allah,ai da fara shafa masa ruwan nan ajikinsa ya fara wani irin motsi da jijjiga ,yana murɗewa ,baffa kuma saiya ci gaba da addu'a yana tofa masa. Ahankali hannun Fattu ya kai kan waɗaɗan na layin dake wuyan macijin nan,aikuwa damƙarsu tayi da Bismillah ta fizge da ƙarfin gaske. ________________Wata irin ƙara da guguwa ne masu matuƙar ƙarfi da firgitarwa , suka cika dakin.ta yadda koda tafin hannunka baka iya gani tsabar duhun da ɗakin yayi,ga guguwa sai juyawa take aɗakin. Ko kaɗan hakan bai tsorata baffa ba ,saima cigaba da yayi da karanto ayoyin shifa daga cikin alƙur'ani mai girma yana tofawa asaitin dayasan macijin nan yana gurin ,duk da duhun daya mamaye ɗakin. Fattu kuwa wani irin tsorone da fargabar suka baibayeta , jin yadda macijin nan yake wata irin murɗewa da sakin wani sautin ƙara mai ban tsoro ,sannna kuma sai takejin yana ƙara mata nauyi sosai akan cinyarta. Cikin tsoro da ruɗewa ta lalubo hannun baffa tace " wayyo baffa tsoro nakeji,wllh kamar yana rikiɗewa ne zuwa wata halittar ,yayimin nauyi akan cinyata baffa, baffa ina tsoron kar wani abu ya faru"Fattu ta faɗa cikin rawar murya mai cike da tsoro. Hannunta baffa ya riƙe shima cikin yanayi na son kwantar mata da hankali yace"karki damu Fattu ba abinda zai faru sai alkairi,kici gaba da karanto addu'oi kina tofa masa in Sha Allah komai yazo ƙarshe "baffa ya faɗi hakan tare da ci gaba da karanto zafafan addu'oi yana tofawa macijin. Fattu ma ɗaurewa tayi taci gaba da karanto addu'ar tana tofamasa, jikinta sai rawa yake,yadda takejin alamun sauyin halittar da macijin nan keyi.idanunta arufe gam-gam. Kusan shuɗewar mintina biyar zuwa bakwai, duhun nan ya fara yayewa ,ahankali hasken tocilolin su baffa ya fara gauraye dakin. Salati baffa ya farayi da ƙarfi da kiran sunayen Allah yana mai kabbara. "La'ilaha illallah muhammadur rasulullahi sallallahu alaihi wasallam,ya Allahu Ya rahmanu ,ya hayyu ,ya ƙayyum,Allahu akbar, Allahu akbar "abinda baffa keta faman faɗi kenan cike da ta'ajibi da jinjina wa ƙudurar Ubangiji,cikin hanzari ya janyo zanin rufuwarsa ya lulluɓawa maciji ,daga cikinsa zuwa ƙasansa dan ba kaya ajikinsa. Jin yadda baffa ke tafaman kabbara da salati ne ,yasa Fattu buɗe idanunta cikin nutsuwa da kuma jarumta ,har zuwa lokacin bata fasa karanto addu'oi ba.akan fuskar baffa ta sauƙe idanunta ,gaba ɗaya baffa ya shiga al'ajabi da mamakin abinda idanunsa suka gane masa.dan har lokacin yana kallon macijin ne ƙuri kamar ya sami talabijin. Ahankali Fattu take sauƙe idanunta zuwa kan cinyarta,wata irin bugawa zuciyarta tayi ,lokaci ɗaya komai nata ya tsaya cak. Sai wata irin rawa da jikinta ya kama kamar zata karkarye,ta ɗauki kusan minti biyu cikin wannan halin kafin taja wani dogon numfashi tana mai buɗe baki tace"ba.....f..ff..fa ...mumm.......tttuummm....nnnee.....a..Mamman.cc.....iiii.....sai kawai ta sulale ta faɗi ƙasa daga zaunen da take. Ba komai bane ya sanya Fattu shiga cikin wannan halin ba , face ganin wani zankaɗeɗen haɗaɗden saurayi ,fari ƙal-ƙal da tayi kwance ya kifa cikinsa akan cinyarta,maimakon macijin dake kwance akan cinyar ta ta. Kuma wannan shine dalilin salati da baffa keta rafkawa cikin kushu'i da tsarkake baiwa da buwayar mahalicci.lallai duniya ta zama abinda tazama ,yanzu mutum ne aka mayar dashi dabba?maciji?kuma ga dukkan alamu wannan ba ɗan yankin nan bane ,dan ko kaɗan baiyi kama da mutanen mu ba. Ahankali baffa yayi kokarin janye shi daga kan cinyar fattu ya kwantar dashi rigingine akan tabarmar. Hannu baffa ya sanya ya gyara masa zanin daya lulluɓa masa dan rufe masa al'aurarsa.sannan ya ture gashin daya lulluɓe fuskar mutumin. "Masha Allah ,watabarakallahu fi ahsanil kaliƙin"baffa ya faɗa adaidai lokacin da yayi arba da fuskar kyakyakywan matashin mai cike da haiba da kwarjini,ga kyan zati. Kallonsa baffa yake ƙuri yana jinjina kai cike da mamaki da alhini,lallai duniya abin tsoroce, rayuwa bata da tabbas,Allah ka karemu,ka rabamu da sharrin maƙiya da mahassada. Baffa ya faɗa acikin zuciyarsa yana kallon bawan Allahn. Ruwa baffa ya ɗebo ya yayyafawa fattu ,ahankali ta fara motsi tana buɗe idanunta ,tar ta buɗe idanun ta sauƙesu akan baffa, kusan minti biyu tana kallon baffa. "Sannu Fattu kinji?tashi ki zauna kiga ikon Allah ,tashi kiga taimakon da kikayiwa rayuwar wannan bawan Allahn. Baffa ya faɗa yana nuna mata inda macijinta yake kwance. Zabura tayi ta tashi zaune cikin tsoro tana kallon inda baffa ya nuna mata,da sauri ta matso kusa da baffa ta riƙe shi gamm! Jikinta sai rawa yake tace "na shiga uku baffa wllh aljani ne wannan ba mutum bane, daga maciji ya koma siffar mutum ,baffa wllh bamu san me zai koma ba nan gaba ,baffa atsorace nake"ta faɗa idanunta yana zubar da hawaye. Ahankali baffa ya kamo hannunta yace "habaFattun baffa ,kin manta ne?macijin nan ne fa ,wanda yake taimakonki cikin hukuncin ubangiji, shine kuma kikejin tsoro yanzu?kin manta da halaccin sa gareki?meyasa bazaki tsaya tare dashiba?alokacin da yake buƙatar taimakonki kema?ki kwantar da hankalinki Fattu ina ji ajikina wannan bawan Allah shine zai zame miki bango kuma tsanin da zai haɗaki da innarki"baffa ya faɗa cikin yanayi na son kwantar mata da hankali. Murmushi Fattu tayi cikin kwarin guiwa tace "hakane baffa ,kuma zan kula da bawan Allahn nan in Sha Allahu ,harya sami lafiya"ta faɗa cikin kwarin guiwa,saidai har zuwa lokacin tsorone fal cikin ranta.ahankali ta matsa kusa da macijin saidai can nesa kaɗan dashi ta zauna . Kallonsa take cike da mamakin tsantsar kyan da Allah yayiwa wannan bawan nashi, ita kam tunda take arayuwarta, bata taɓa ganin wani mutum mai kyan wannan bawan Allah ba. Dan duk kyanta da ake faɗa ,tayi imani bata kama koda ƙafar wannan bawan Allahn ba. Ahankali ya fara motsi yana ɗan juya kansa hagu da dama.sai kuma ya fara ɗan fizge fizge kamar yana ƙoƙarin tuna wani abunne ko kuma yana son farkawa daga wani mummunan mafarkin . "Baffa kaga abinda yake "Fattu ta faɗa cikin zabura tana kallon baffan. Wata yar jarka baffa ya ɗauko ya buɗe ,ahankali yafara shafa masa ruwan dake cikin jarkar. ahankali maciji ya sauƙe wata ajiyar zuciya mai ƙarfi yana sauƙe numfashi ahankali ahankali. Addu'oi baffa yake tayi cikin wasu magunguna kala-kala yana shafawa bawan Allah nan da yake kwance ,wanda zuwa yanzu jikinsa yayi sanyi,ba kamar dazu da yayi zafi ƙau-ƙau ba. Tun daga ƙafafuwansa Fattu ke kallonsa har zuwa fuskarsa,masha Allah. Wannan mutumin ya haɗu ta ko ina ,anya ma wannan ba haushene?ko bafulatanine irin mu?kai gaskiya wannan bayajin Hausa ko fulatanci,ohhh Ni Fattu yanzu wanann macijina ne haka ?dama da mutum nake ma'amula ashe?waye wannan bawan Allahn?su waye sukayi masa wannan shirin haka?me yayi musu ?inane garinsu?meye sunansa?waɗan nan sune tambayoyin da Fattu ke buƙatar amsarsu ,saidai ba mai bata amsar sai wannan bawan Allah. Baffa ma tunani yake wannan bawan Allah daga ina yake? ,waye yayi masa wannan sihiri?koma dai menene yayi masa maganin da duk sihirin mutum bazai yi tasiri akanshi ba da yardar Allah. Suna nan zaune jigum jigum, cike da fatan Allah yasa ya farka ba tare da wata matsalar ba,kawai suka ga ya fara motsi karo na biyu,saidai wannan karon ba fizge -fizgen yake ba ,kawai dai ya ɗan riƙe kansa yana kuma yatsina fuska. Ido suka ƙura masa ba wanda yayi magana ,daga Fattu har baffa,kowa yayi shiru yana kallon ikon Allah. Ahankali bawan Allahn nan ya fara bude idanunsa yana ɗan lumshesu ,kafin ya buɗe su tar kamar lantarki dan tsananin haske da sheƙin da suke yi. Ƙur ya ƙure rufi bukkar dakin baffa da idanu,baya ko ƙiftasu,tunani yake ina ne nan?waye ya kawo shi nan?kuma yaushema suka zo nan ɗin? Yunƙurawa yayi ya tashi zaune ahankali yana cije light pink lips ɗinsa .kallon ɗakin yake cike da mamaki ,har ya juyo zuwa inda su baffa ke zaune shida Fattu sunyi masa ƙuri suna kallonsa,baffa ya fara kalla cike da rashin sani. "Sannu bawan Allah ka tashi ?meke maka ciwo yanzu ?me kake ji ajikinka" baffa ya faɗa lokacin da suka haɗa ido da bawan Allahn . Ahankali bawan Allahn ya lumshe idanunsa tare da jingina da jikin bangon ɗakin.yana mai dafe kansa ,dan ciwo yake masa sosai. "Ayya Fattu inaga fa wannan bayajin hausa ,kuma bayajin filatanci miƙamin wannan kwaryar In bashi magani ,da alama kanshi ke ciwo. Cewar baffa kenan, dayaji yayi magana amma bawan Allahn bai bashi amsaba. Ahankali Fattu ta miƙe ta ɗauki kwaryar ta miƙawa baffa ita ,tana mai cewa "baffa gashi,kuma kamar ma yana jin yunwa ko ?kaga yana shafa cikinsa"ta faɗa tana kallon yadda bawan Allah ke shafa cikinsa zuwa ƙirjinsa wanda gashi yayi kwance luf-luf akai. Ahankali bawan Allah ya ɗago kansa yana kallon saitin dayaji sassanyar muryar Fattu na tashi. Aikuwa karaf idanunsa suka gauraye cikin na juna ,wata irin faɗuwar gabace ta ziyarcesu alokaci guda, da sauri bawan Allahn ya kawar da kansa yana mai dafe ƙirjinsa,dan sosai ƙirjinsa ya buga. Bangaren Fattu ma kuwa,wata irin bugawa ƙirjinta yayi, wacce har saida taji numfashinta ya ɗauke ,wani jiri ne ya ɗebeta ,tayi baya luuuuuuu zata faɗi,ƙara ta kwalla cike da jin tsoro tana mai runtse idanunta, saidai kuma kafin ta kai ƙasan taji ta faɗa kan wani lallausan abu mai kama da katifa tsabar laushi. Ahankali ta buɗe idonta ta sauƙesu akan......... Muje zuwa masu karatu yanzu muka fara. Taku ce dai anty mammy Mrs babi💘💘 Share and comment fisabilillah More comment More typing. [7/15, 9:37 AM] +234 906 568 0805: 🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄 MACIJI NE🪱🪱🪱 Na mammy kabeer (Anty mammy) Elegant online writers📚📚 Free book Page 17/18 ______________Ƙara fattu ta kwalla cike da tsoro,dan ta saddaƙar kawai ta gama faɗuwa,saidai kuma maimakon tajita akan ƙasa ,saitaji ta faɗa kan wani abu mai matuƙar taushi kamar katifa. Da sauri ta buɗe idanunta dan ganin inda ta faɗa,cikin mamaki take kallon bawan Allah nan,dan hannunsa ta faɗo, lokacin da yaga tayi baya zata faɗi ,bai ma san lokacin daya zabura yayi kanta ba ,tare da tareta ta faɗo akan hannunsa . Kallon kallon sukewa juna basa ko ƙiftawa, yayin da bawan Allah ya zazzaro idanu waje ,irin wanda idan mutum yaga abin tsoro ɗin nan. Ita kuma fattu mamaki take yaushe ya taso yazo gareta harya tare ta ?bata kai ga faɗuwa ƙasa ba? Baffa ne yayi gyaran murya tare da faɗin "subhanallah,fattu sannu, Allah ya taƙaita wahala da tuni kin faɗin ƙasa ,bawan Allah sannu kaji,kana fama da kanka amma zuciyarka mai tsafta bazata bari wani ya cituba,ina mai godiya gareka"baffa ya faɗa cike da jinjinawa bawan Allah nan,lallai akwai wani abu da Allah ya ɓoye tsakaninsa da fattunsa, haƙiƙa fattu kam,zuwa yanzu ta sami mai taimako,kuma yanzu ne ya kamata su fara neman dangin Fattu ,dan zuciyarsa na raya masa wannan bawan Allah alkairine ga rayuwar fattunsa. Ahankali bawan Allah ya miƙar da fattu tsaye ,yana kallon ta sai dai fuskarsa sam ba walwala ,da alama dai irin mutanen nan ne marasa yawan fara'a . Fattu kuwa da sauri ta juya baya tana mai dafe ƙirji ,dan hango zanin da baffanta ya lulluɓawa mutumin a ƙasa,kuma da alama bai ma san zanin ya daɗi ƙasanba. Da sauri shima ya ankare cewar ba zanin fa ajikinsa ,wato yana tsaye tsirara ne.cikin azama ya durƙusa ya ɗauki zanin yana cukuikuyewa ajikinsa, idonsa akan fattu yana fatan Allah dai yasa wannan yarinyar bata ganshi haka ba,dan ma dakin ba wani haske sosai.dan tocilolin sun kalli wani direction ɗin ne da ban. Zama yayi cike da jin haushin yadda zanin jikin nashi ya daɗi kasa,wai ma to ina kayansa ne?me yasa y ganshi haka ba kaya ne? Daga kanshi yayi yana kallon baffa daya miƙa masa kwaryar da fattu ta miƙa dan abashi magani. Karɓa yayi shikam nadan yasan menene aciki ba , kallo yabo kwaryar dashi,yana jin wani irin tashin zuciya ,dan kwaryar ta tsufa sosai ,tayi baƙi saboda ruwam rubutun da ake zubawa a cikinta. "Maza ka shanye bawan Allah zakaji sauƙin ciwon kan"baffa ya faɗa yana nuna masa alamun ya sha da hannunsa ,dan gani yake kamar bayajin me suke faɗi. Kafa kansa yayi yana shan maganin ,bayan ya runtse idanunsa.saida ya ɗansha da yawa kafin ya miƙawa baffa kwaryar. Saidai ko minti ɗaya baiyi da sha ba ,ya kama yunƙirin amai.aikuwa tasss ya mayar da maganin nan,sannu kawai baffa ke masa. Juyowa fattu tayi lokacin daya fara aman, dan tunda ta juya musu baya bata ƙara juyowa ba,saida taji yana aman. Ahankali ta buɗe bakinta tace "sannu hamma"ta faɗa ahankali. Kallonta yayi ,tare da kawar da kansa can gefe yana jingina da jikin katangar karan,ba tare da yayi magana ba .itama bata damu da sai yayi maganar ba,dan su tunaninsu bayajin me suke faɗi. Cikin nutsuwa fattu ta gyara gurin da yayi aman,kanta aduke ,har zuwa lokacin gabanta yaɗuwa yake .shi kuwa bawan Allahn nan yana daga jikin bango Ya lumshe idanunsa ,kamar mai barci.saidai duk abinda fattu keyi idonsa na kanta,mamaki yake da irin kyan da yarinyar ke dashi,gata da nutsuwa komai nata gwanin burgewa.tana da hankali bata da rawar kai duk da ƙaranci irin na shekarunta.dan ya san wannan bata wuce 14/15ba amma Masha Allah,tana kyan diri irin na cikakkun mata ,kalli hips ɗinta kamar wanda aka ɗora mata shi Dass abinta. Jikin fattu ne kawai ya bata cewar kallo ta mutumin nan keyi,dan haka ahankali ta ɗago kanta ,shikuwa daidai lokacin ya ɗan ƙara buɗe idanunsa yana kallon ɗan ma dai-dai cin lips ɗin ta, masu taushi , sai sheƙi suke.aikuwa carab ta kama shi yana mata kallon ƙurillah. Ɗan hararar ta yayi tare da kawar da kansa ,aransa yace "wannan ta cika kallon mutane " Kuji fa masu karatu ?ko tsakanin shi da fattun wake kallon wani? Da sauri fattu ma ta kawar da kanta,azuciyarta tana mai cewa "kuji min mutum shi yana kallon mutane amma kuma baya son akalleshi" "Abba waye yakawoni nan?kuma me nakeyi anan?sannan kuma ina kayan? Baffa da fattu suka ci tsinkayi murya mai shegen daɗi da amon sauti cikin nutsuwa.da mamaki gaba ɗaya suka bishi da kallon ,ba wanda yayi magana dan sai sukaga kamar bashi yayi maganar ba ,dan yana yadda yake bai ko buɗe idonsa ba lokacin da yayi maganar. Jin sunyi shuri ba wanda yayi magana ne ,yasa bawan Allah buɗe idanunsa da suka ɗan yi ja kaɗan yana kallon baffa,sannan ya ƙara maimaita tambayarsa cikin Hausarsa da bata fita sosai. "Ashsha -ashsha ikon Allah yaro ashe kana jin Yaren Hausa ?Alhmdllh.sannu kaji bari na baka kaya saika saka,inyaso zuwa wayewar gari nayi magana kaji"baffa ya faɗa yana mai buɗe wata tsohuwar bakonsa ,kaya ya daukowa bawan Allah nan ,waɗanda dasu yake zuwa sallar juma 'a .wani yaɗi ne yollow share dashi ,anyi masa ɗinkin riga da wando dogaye .miƙa masa baffa yayi yace "kasa Waɗan nan tukunna yanzu kaji" Karɓar kayan yayi yana mai ƙare musu kallo,to ina nashi kayan da za'a bashi Waɗan nan kayan wani iri dasu haka?ɗari kansa yayi ya kalli baffa yana son yayi magana ,amma sam ya kasa,dan ba ɗabi'arsa bace yawan magana ,yana matuƙar jin wahalar yin magana ,shiyasama tun farko yaƙiyi musu magana . Kallon fattu yayi wacce ke zaune can nesa dasu kanta aduƙe,tana wasa da yatsun hannunta ,sannan ya kalli baffa ,ya kalli kayan hannunsa kuma . Fahimta baffa yayi cewar ,yana son saka kayan ne ,kuma yana buƙatar fattu ta bar gurin,dan haka baffa yace "fattu muɗan bashi guri ya kimtsa ko"baffa ya faɗa yana mai kama hannun fattun sukayi wajen ɗakin. Bayan fitarsu daga ɗakin,shikuwa kallon yabo kayan dashi yana juyasu ahannunsa, kusan minti uku kafin ya saka rigar ,dube dube yake ko zaiga boxern sa ,saidai ba alamun boxer aɗakin nan,dan haka ya saka wando yana mai turo baki da ɗan yamutse fuska.sauƙinsa ma ɗaya kayan wanke suke tas ɗasu,sai ƙamshin kilin suke.lol. Koda ya saka kayan zamansa yayi a inda ya tashi tare da lumshe idanunsa ya faɗa duniyar tunani ,shikam a iya tunaninsa baisan meye dangantakar da da Waɗan nan mutanen ba,abinda zuciyarsa tafi yarda dashi shine,wata ƙila yayi hadarine suka ganshi suka taimakeshi. Baffa ne yaji shiru baice musu ya kammala saka kayan ba,kuma ga fattu sai rawar ɗari take, dan zuwa wannan lokacin an jima da ɗauke ruwan saman da ake tsugawa,dare ya raba sosai. Dan haka saiya ɗan leƙa cikin ɗakin.aikuwa azaune ya hangoshi ya jingina kansa da jikin katanga ,sannan idanunsa alumshe . "Ayya ashe ma ya ida shiryawa fattu, shigo daga ciki kar mura ta mamaki naga kinata rawar sanyi,bana so kije ɗakinki ki kwanta saboda hansai idan ta ganki zata je ta sanar da lamiɗo kina nan"baffa ya faɗa yana mai tura ƙofar dakin nashi ya rufeta. "Sannu bawan Allah"baffa ya faɗa cike da tausaya wa. Jinjina kai kawai bawan Allah yayi ,ba tare da ya buɗe idonsa ba. Zama baffa ya gyara ya ƙara cewa"ko zaka iya tuna wani abu daya danganci rayuwarka"?ya faɗa cike da fatan cewar bawan Allah nan bai manta komai na rayuwarsa ba. "Ikon Allah ,saikace wanda yayi lossing memery zan manta da rayuwata "bawan Allahn ya faɗa cikin ransa,amma a zahiri ,ɗan buɗe idonsa yayi ya kalli baffa,sannan ya maida idonsa kan fuskar fattu wacce itama shi take kallon kamar ta sami talabijin. "Kai wannan yarinyar ta cika kallo wllhda wani idanunta masu kama da ruwan Gwale"ya faɗa cikin zuciyarsa yana mai hararar fattun ,kafin ya ɗauke idanunsa daga kanta ya maida kan baffa . Saida ya kai kusan minti biyu kafin ya buɗe baki ahankali kamar baya so yace "my name is ADEEB MUHAMMAD ASHRAF "ya faɗa yana jinjina kansa tare da kallon baffa.gani yayi baffa yana kallonsa alamun kamar bai fahimceshiba. Lumshe idonsa yayi cike da gajiya ,sannan yace "sunana ADEEB MUHAMMAD ASHRAF"yana faɗin haka ya mayar da kansa ya jingina tare da lumshe idanunsa. "To- to masha Allah malam Adeeb ina ne garinku ? Baffa ya faɗa cikin gamsuwa da jin cewar shiɗin musulmine. Dan da yana ta kokwanto shin musulmi ne shi ko arne? Amma zuwa yanzu ya sami nutsuwar jin cewa shiɗin musulmine. Shiru yayi kamar bazai yi magana ba, kafin ya buɗe baki yacewa baffa"nidan MISRA ne" ya faɗa yana kallon yadda baffa yayi zugum cike da tunanin ina yakejin Misra? "Ikon Allah malam adeeb duk da dai Ni ba sanin Misra a ina take nayi ba,amma nasan garine mai matuƙar nisa ,to zahiri gaskiya nan kana Nigeria ne ,cikin ƙauyen ƴar ruga dake jahar Gombe"baffa ya faɗa yana kallon Adeeb wanda mamaki ya mamaye ilahirin fuskarsa , Nigeria kuma ?yaushe yazo Nigeria?bayan rabo da da Nigeria tun last year? "Who brought me hare"?ya faɗa cikin mamaki da sanyin murya.sai kuma ya ɗan rufe idonsa tare da dage kansa kafin yace "waye ya kawoni nan? Shiru baffa yayi ba tare da yace komai ba,na tsawon lokaci ,kafin ahankali ya nuna masa fattu yana mai cewa"haƙika wannan yarinyar itace solar haɗuwar mu dakai ,kuma anan garin ta ganka -----nan dai baffa ya bashi labarin abinda ya sani ,da kuma abinda ya faru yanzu harya koma asalin halittar da. Tunda baffa ke magana Adeeb ya saki baki yana kallo da sauraron baffa,mamaki yake wai shine ya zama maciji?as how ? Me ya faru dashi ?waye ya maida shi hakan?ya Allah who's known how long yake cikin garin nan,ko yaya ƴan gidansu? Ko wane hali suke ciki yanzu?yasan yanzu haka hankalin amminsa yayi matuƙar tashi fiye dana kowa ,lallai dole ya bar garin nan ko ta halin ƙaƙa. "Na gode sosai da taimakon rayuwata da kuka ,amma bani da wani masaniya akan abinda ya sameni, ina don barin garin nan gobe-dan akwai gagarumin abinda ke gabansa,saidai i promise you I will get you back,zan dawo gareku"ya faɗa cikin wani irin yanayi na ban tausayi,dan gaba ɗaya jikinsa asanyaye yake ,sannan damuwa ta cika fuskarsa taf! Da gani maganar ta shiga jikinsa sosai . Cikin murmushi baffa yace ba komai malam Adeeb Allah yayi mana jagora ,saidai ina neman alfarma agareka"baffa ya faɗa cikin damuwa. "Ba komai Abba ka faɗi duk abinda kake don faɗi and I promise zanyi maka shi"ya faɗa cikin sanyin murya mai cike da tarin damuwa. "So nake ka tafi da ƙanwarka can garin naku ,domin ka taimaka mata wajen saduwa da asalin iyayenta baffa ya faɗa cikin tsantsar damuwa yana mai kallon fattu,wacce taji maganar baffa kamar sauƙar aradu ....... Masu karatu mu tara next page Taku ce anty mammy Mrs babi💘💘 Share and comment fisabilillah. [7/15, 9:54 PM] +234 906 568 0805: 🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄 MACIJI NE🪱🪱🪱 Na mammy kabeer (Anty mammy) Elegant online writers📚📚 Free book Page 19/20 https://www.facebook.com/groups/1627491150723081/?ref=share_group_link Masu amfani da face book sai kuyi join wannan group ɗin . _______________"So nake ka tafi da ƙanwarka can garin naku,dan taimaka mata wajen gano iyayenta na asali"baffa ya faɗa yana kallon fattu ,wacce tunda baffa ya fara maganar take jin wani irin matsanancin faɗuwar gaba ,ji tayi maganar tasa ta sauƙa acikin tsakiyar kanta ,kamar sauƙar aradu,"wace irin magana baffa keyi ne haka" anya kuwa yasan me yake faɗi?kai a'a gaskiya bai gane me yake faɗi ba shima. Fattu ta faɗa cikin zuciyarta,tana mai sauƙe ajiyar zuciya ,dan ta fahimci baffa yana nufin innar ta kenan,saidai kuma bata da wani dalilin bin mutumin da bata sanshi ba,Gara tayi zamanta agurin baffanta ,inyaso innar tata inhar ta damu da ita ,zata zo gareta. Ahankali fattu ta buɗe bakinta tace "baffa ina ganin babu buƙatar saina bishi wani garin ,dan neman innata,zan zauna anan ɗin idan da rabon zamu gana wata rana zata zo gareni baffa"fattu ta ƙare maganarta cike da mugun bugawar zuciya ,dan har lokacin kalaman baffa na mata yawo akanta. Ajiyar zuciya baffa ya sauƙe cike da alhini abinda zai faɗa wa fattun ,kafin yace"ayya fattu amm ki saurareni, da kyau ,ki nutsu ,kuma ki sani kowane bawa da yadda ƙaddararsa ke zuwa masa. Haƙiƙa Ni malam bukar bani ne na haife ki ba na tsincekine tun kina yarinya ƙarama "baffa ya faɗi hakan yana mai sunkuyar da kansa cike da tausayin fattu. "Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un baffa me kake faɗi ne haka?dan Allah baffa kayi haƙiri idan nayi maka wani laifin ne,amma karka ƙara nesanta alaƙarka dani, baffa bazan iya jura ba,bansan kowa ba sai kai ,kai kaɗai ne gata na baffa dan Allah karka rabu dani "fattu ta faɗa cikin matsanancin kuka marar sauti sosai. Shide Adeeb kallonsu kawai yake cike da mamaki,how can that be possible ace wai ya tafi da wata yarinya har can ƙasar su ,yace a ina ya samota ?kuma ta yaya ma zai fara neman ahalin yarinyar .shifa gaba ɗayama lamarinsu ɗaure masa kai yake ,basu sanshi ba,ba wata alaƙa atsakaninsu dashi,amma yana ƙoƙarin bashi yarinya ya tafi da ita. Kallon baffa yayi lokacin dayaji yana magana da cewa"nasan zaki shiga ruɗu da damuwa Aduk lokacin da kika sami wannan labarin fattu,saidai bani da yadda zanyi,yazama dole insanar dake gaskiyar abinda ke wakana,kisani fattu ina ƙaunarki fiye da ƴaƴan dana haifa na cikina dan kin fiyemin su sau dubu.amma son da nake miki bazai sa in cutar dake ba ta hanyar ƙin faɗa miki gaskiya fattu , kisani ahalin yanzu zamanki arugar nan akwai haɗari ,idan mai gari ya farka,kinsan hukuncin da zai zartar akanki bazai mana daɗi ba .dan haka kiyi haƙuri wllh badan cutarwa yasa nace tafi dake ba,saidan ko da baya nan to nayi niyar barin garin nan dake Dan tseratar da rayuwarki" Baffa ya faɗa hawaye na zubowa daga idanunsa. Kuka fattu kawai take cike da wani irin baƙin ciki marar misaltuwa, wannan wace irin ƙaddara ce ?yanzu shikenan bata ga tsuntsu bata ga tsarki,baffan da take gani matsayin mahaifinta ashe shima ba mahaifinta bane?kenan ita bata da kowa?tunda ta taso take cikin bakin ciki da damuwa ,amma ta kwance zamanta cikin wannan bakin cikin akan zuwan wannan ranar.kuka take irin wanda yake fitowa kai tsaye daga zuciya ba abinda take fata ahalin yanzu kamar ace ta farka taga ashe barci take ,tayi wannan mummunan mafarkin.to suwaye iyayenta?me tayi musu suka yarda ita?shin basa son tane ko yaya?tambayar da take tayiwa zuciyarta kenan,jikinta kuwa nan da nan ya ɗau ɓari,kan kace me tuni zazzaɓi mai zafi ya kamata. Ahankali Adeeb ya kalli baffa na tsawon lokaci kafin ya buɗe baki cikin salonsa na rashin son magana yace "amma Abba ta yaya zaka bani ƴarka i tafi da ita ?bayan baka Sanni ba,bakasan koni ɗin waye ba ,infact baka saniba ma koniɗin mugune ,Amma kake don bani ƴarka in tafi da ita why?Adeeb ya faɗa yana kallon baffa. Dan murmushi baffa yayi,irin wanda yafi kuka ciwon nan,kafin yace "na yarda da kai nasan bazaka taɓa cutar min da fattu ba ,dan tun kana wata halittar wacce ta kasance muguwa kake taimakonta, bare yanzu da kake cikakken mutum.sannan na jima ina addu'a akan Allah ya kawo wanda zai zama silar farin cikin fattu ,sai haka Allah ya kawo ka,alokacin da mu bamuyi tsammani ba,kuma kallo ɗaya nayi maka zuciyata ta aminta da kai ,nasan Allah ne ya karɓi addu'a ta.dan haka bani da wani kokwanto akanka." Baffa ta faɗa cikin nuna yanayi na gamsuwa akan hukuncin daya yanke. Ahankali fattu ta rarrafe zuwa kusa da baffa ,hannunsa ta kama ta riƙe gamm!cikin nata ,kafin tace "baffa su waye iyayen nawa?me yasa suka yarda Ni?a ina ka tsinceni?ta faɗa cikin kuka tana mai jan majina. Kallon ta Adeeb yayi cike da tausayawa,dan sosai yaji ta bashi tausayi, she's too young ace ta fuskanci wannan babban ƙalubalen. Baffa ne ya fara magana da cewa"kafin na auri hansai na auri wata kanwata,yar gidan tayar babata. Inda muka kasance duka marayune daga i har ita.itace matata ta farko ,minyi aurene irin na haɗin zumunci,tana da haƙuri da kawaici ,muna zaune cikin aminci da mutunta juna,har Allah ya bata ciki. Munyi murna sosai da samun wannan cikin ,tare da addu'ar Allah ya sauƙeta lafiya. Wata rana kuwa naƙuda ta kamata,ganin yadda take shan wahala ,saina tafi jeji dan ɗebo mata maganin gargajiya tasha,ina cikin tafiya nayi nisa sosai da rugar nan,kwatsam saina fara jiyo kukan jariri,haka nayi ta bin sautin kukan harna cimma gurin. Kwance na iskeki kinata kuka gaba ɗaya jikinki yayi ƙura, sannan kin kukkurje dan ga jini jini nan ma ajikin rigar dake jikinki, Addu'a nayi tare da ɗaukoki na dawo gida . Koda na dawo gida na iske matata tana kuka ga gawar jaririya nan gabanta.wato ƴar da ta haifa ta koma. Munyi baƙin ciki sosai da rashin yarinyarmu,amma haka muka haƙura muka mikawa Allah lamarinmu. Nan na bata labarin samoki da nayi,sai naga tana ta murna da farin ciki,batayi wata- wata ba ta karɓe ki ta fara shayar dake,koda nayi magana saitace"Allah ne ya dawo mana da farin cikinmu.dan haka zamu rikeki matsayin ƴarmu da muka rasa,idan kuma munji anyi cigiyarki saimu bada ke. Nan da nan nima na yarda da shawarar ta ,dan lokaci ɗaya Allah ya samun ƙaunarki raina. Haka na gayyato mutane akayi suturar ƴarmu,yayinda nake faɗawa Mutane cewar ƴan biyu matata ta haifa ,ɗayar ta koma sai ɗayar. Lokacin da muka tsinceki akwai wani sarƙa awuyanki,wacce da alama zata yi matukar tsada ,dan haka sai muka cire muka ajiyeta haɗe da rigar dana tsinceki da ita. Munsha tambaya akan ya akayi baki biyo ko ɗaya daga cikinmuba,dan kin kasance kyakyakywa wacce kaf rugar nan ba wanda ya kama ƙafar kyanki,sannan gashinki ba irin namu bane.haka dai muke samun amsar da zamu rufe bakin mutane da ita. Shekararki biyu a duniya ,Maryama ta koma ga Allah.munyi kuka daga ni harke na rashinta, kafin daga bisani muka haƙura. Lokacin ne na auri hansai ,wacce ta kasance ba abinda ta iya banda mugunta da baƙin hali,sam bata ƙaunar ki ,da idan tayi miki wani abun nakan yi magana ,saidai daga baya kuma sainake kasa yin maganar,koda na yunƙuro da nufin yin maganar bana iyawa. Wannan shine taƙaitaccen tarihinki fattu na.amma na tabbata ko ba daɗe ko ba jima zaki haɗu da asalin iyayenki,jikina yana bani kun kusan haɗuwa. Wanda idan har kikaci gaba da zama cikin rugarnan, hakan bazata faru ba.zan nemeki Aduk inda kuke fattu na "baffa ya faɗa cikin kuka abin tausayi. Fattu ma kuka take sosai kamar ranta zai fita ,"baffa ina sarƙar take "fattu ta faɗa cikin rawar murya irin ta mai zazzaɓi. Tashi baffa yayi ya buɗe cikin jakarsa ta kaya ya ɗauko wata leda ya kunce,saiga wata sarƙa mai tsananin sheki da ɗaukar ido,sai wata ƴar riga mai kyau fara ta yara.miƙawa fattu kayan baffa yayi . Ahankali ta karbi kayan ta rungume ajikinta tana kuka mai tsuma zuciyar mai sauraro. Kallonsu kawai Adeeb yake ,dan zuwa yanzu ya gama ɗaukarwa kansa alƙawarin taimakawa fattu ta kowace fuska ,har saita ga iyayenta. Baffa kansa kukan yake ,yana jimamim rabuwa da Fattun sa. Tashi Adeeb yayi ,cikin tafiyarsa ta izza da cike jarumta ya ƙarasa kusa da fattu ,tsugunmawa yayi akusa da ita ,yana kallon fuskarta dake ta faman kuka ,gaba ɗaya tayi jajur da ita. Hannunsa ya sanya ya ɗago habarta ya kura mata ido,buɗe idanunta tayi itama ta sauƙe cikin nashi,sun ɗauki kusan mintuna uku suna kallon juna,kafin Adeeb ya sauke wani kwauron numfashi ,sannan ya sanya babban ɗan yatsanshi ya share mata hawayen dake zuba a idonta.girgiza mata kai yayi alamun ta daina kuka.amma sam ta kasa dainawa. Sarƙar hannunta ya karɓa yana kallo,sarkar zallar daimond ce sai sirin kwal,da gani wannan sarƙar ta doshi millions ,koma ina yarinyar nan ta fito to tabbas ƴar gidan manya ce,in Sha Allah zai haɗata da iyayenta na asali. Sarƙar ya buɗe tare da nufar wuyanta wanda yake nan zafi ƙau da zazzaɓi,ya ɗaura mata sarƙar.nan da nan sarƙar ta ɗauki wani sheƙi da walwali. Dawo da kallonsa yayi kan baffa wanda yake kallon duk abinda ke faruwa,zuciyarsa tana masa wani irin ƙuna da ciwo. Saida ya ɗauki kusan minti biyar kafin yace "Abba nayi maka alƙawarin zan taimaka wajen neman asalin iyayen yarinyarka,zamuiyi amfani da wannan sarƙa in Sha Allah everything is gonna be ok"ya faɗa cikin muryar sa mai daɗin amo . Hannunsa baffa ya kama cikin farin ciki yace "na gode Allah yayi maka albarka,ka kulamin da fattu karka bari ta cutu " Jinjina kai yayi shima yana mai riƙe hannun baffan, akaro na farko ya ɗanyi murmushi.masha Allah masu karatu bakuga yadda yayi wani sihirtaccen kyau ba,Dan murmushin ba ƙaramin kyau ya ƙara masaba. Kwanciya fattu tayi akan sallaya ta juya bayanta tana ta kuka da rawar zazzaɓi,shikenan yanzu haka zata bi wannan bawan Allah da batasan koshi waye ba,meyasa iyayenta suka yarda ita?me tayi musu haka da zafi?dama baffa ya fasa ƙidurinsa na cewar saitabi wannan bawan Allah mana. Baffa ne ya miƙe tsaye da sauri tare da leƙawa ƙofar ɗakinsa, dan tabbas yaga gilmawar mutum,aikuwa yana leƙawa ya hango zanin gwogwgo hansai tana shigewa ɗakinta. Ya Salam kenan taji duk abinda suke tattaunawa ?lallai dole su bar gidan nan kafin gari ya gama wayewa.dan yanzu kam asuba ta kawo kai, Da sauri ya koma ɗakin yace "Adeeb akwai matsala,yanzu yanzu zaku tashi ku dau hanya,dan kuwa hansai taji duk abinda muke tattauna,kuma na tabbata ko bari bazata yi gari ya gama wayewaba zata je ta sanar da mai gari" Baffa ya faɗa cikin tashin hankali da damuwa. Shikuwa Adeeb ko ajikinsa ƙara gyara zama yayi ,dan bazai iya kwanciya anan gurin ba ,kafin ya kalli baffa ya ɗan taɓe baki yace "and so what idan ta faɗa masa"? Ya faɗa cikin ko in kula. "Bazaka gane zalumcin lamiɗo ba Adeeb zai iya sawa kashe fattu ,dan Allah ku tashi muje In fitar daku hanya ku tafi, ka taimaka min ka ceci rayuwar yata"baffa ya faɗa cikin kuka yana durƙusa akan gwuiwoyinsa. Da sauri Adeeb ya tashi ya kama baffa ya miƙar dashi yace "is ok Abba zamu tafi yanzu.ya faɗa yana mai kamo hannun fattu ya miƙar da ita tsaye. Ita kuwa fattu yadda yake jin zuciyarta bayani ace mai gari yasa a kasheta Bama,koba komai zata huta da ƙuncin zuciya da damuwa.tana mikewa tayi baya zata faɗi,dan gaba ɗaya ba ƙarfi ajikinta.da sauri Adeeb ya tallafi ga zuwa jikinsa,kallon fuskarta yayi wacce ta kumbura ,sai rufe idanu take tana buɗe wa,da gani tana shan jiki sosai. "Muje bawan Allah ,fattu daure kinji"baffa ya faɗa cikin ruɗu ,ba abinda yake ɓukata irin yaga sun bar rugar nan. Ganin fattu zata ɓata musu lokacine yasa Adeeb ya ɗagata sama tsak!kamar ƴar tsana ya saba akafaɗarsa yacewa baffa" muke Abba" Wata leda Baffa ya dauko,tare da rigar nan ta fattu ya cusa ciki,sannan yayi waje suka rufa masa baya...... Masu karatu me zakuce game da rabuwar baffa da fattu? Mrs babi ce💘💘 [7/17, 6:48 AM] +234 906 568 0805: 🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄 MACIJI NE🪱🪱🪱 Na mammy kabeer (Anty mammy) Elegant online writers📚📚 Free book Page 21/22 _______________Wata leda Baffa ya ɗauko ,ledar da ɗan nauyi ,alamun wani abune acikin ta .sannan ya ɗauki wannan rigar ta fattu ya cusa acikin ledar,safin yayi waje ,Abeed ya rufa masa baya. Ahankali baffa ke takawa Abeed na biye dashi,saɓe da fattu akafaɗarsa,wacce ke cikin matsanancin hali na zazzaɓi,da damuwa. Tafiya suke cikin sauri bayan sun bar gidan ,cikin ikon Allah basu haɗu da kowa ba ,har sukayi nisa da garin sosai,saida baffa ya fitar dasu kan kwalta kafin ya tsaya . Har zuwa wannan lokacin fattu na saɓe akan kafaɗar Abeed ,duk da irin uban nisan dake tsakanin rugar da kwalta. Ahankali Abeed ya sauƙe fattu ya ɗan jingina ta da jikinsa,dan yaga bazata iya tsayuwa ba . "Malam Abeed karɓi wannan wasu yan kudadene da nake tarawa saboda irin wannan ranar,nasan zasu toshe muku wata kafar,dan Allah ka riƙe min alƙawari, ka kulamin da fattuna,karka bari wani ko wata ya cutar da ita,sannan kayi iyakar ƙoƙarin ka wajen sadata da magaifanta. Kaima zaka sami lada"baffa ya faɗa yana kallon bayansa ,hanyar da suka baro ,dan tsoro yake kar yaje ko anbiyosu,dan yasan zuwa yanzu labari ya isa kunnen lamiɗo,tunda gari yayi haske an kusan shiga sallah. "In Sha Allahu Abba zan kula da amanar ka,na gode da taimakon da kukayimin, sannan zan dawo gareka very soon"Abeed ya faɗa cikin nutsuwarsa da rashin son magana,akwai abubuwan da yake son faɗa amma tsabar rashin son maganarsa bazai iya ba dan haka yayi shiru daga wannan maganar. Hannun fattu baffa ya kama yariƙe gam-gam cikin nashi,kallon ta yayi yayinda itama take kallonsa cikin kuka wanda muryarta ko fita batayi sosai, shima baffa tuni zuciyarsa ta karaya ,sai hawaye sharrrr!! "Allah ya shiga lamarin ki fattu, Allah ya karemin ke ka yasa damu da alkairi,ki kula da kanki,ki kama mutuncinsu.Allah yayi miki albarka"baffa ya faɗa cikin kuka sosai,abin tausayi. "Baffa bana son tafiya ,dan Allah kace na zauna ,Ni nafison zama da kai akan iyayena ma asali,baffa karka tafi ka barni "Fattu ta faɗa cikin kuka harda shashsheka kamar zata shiɗe. Kafin baffa yayi magana saiga wata mota zata wuce ,da alama daga cikin Jos take . Da sauri baffa yayi musu hannu alamun su tsaya.tambayarsu yayi ina suka nufa ,mai motar yace Kano. Kallon Adeeb baffa yayi yace "duk da bansan inane Kanon ba amma Gara kubi wannan motar kafin tawagar mai gari su fito nemanku. Kai kawai Abeed ya ɗada,tare da kamo hannun fattu suka nufi motar,hannunsa ɗaya riƙe da ledar da baffa ya basu. Kuka fattu take harda ihu tana faɗin"wayyo baffana ,banason tafiya,dan Allah baffa kace na dawo wayyo baffa am wayyo Allah na ,wayyo rayuwata " Baffa kam ko magana ya kasa tsabar kuka sai daga musu hannu kawai yake yana juya kai. Abeed ne ya sanyata cikin motar tare da riƙe ta ,ɗan sai ƙoƙarin fitowa take ,haka mai motar nan yaja motarsa yayi gaba,dan kaya zaije ɗaukowa. Baffa yana tsaye har saida yaga ɓacewar motar ,sannan ya sauke wani kwauron numfashi yana mai share hawayen idanunsa,"Allah ga amanar ƴata nan na miƙa lamarin ta ahannunka ,ya ubangiji kazama majiɓancin al'amarinta "baffa ya faɗa yana mai juya dan koma gida ayi wacce za'ayi. Aikuwa tun kafin ya ƙarasa cikin garin ,ya hango cincirindon mutane aƙofar gidansa,jinjina kai yayi,dan dama yayi tsammanin hakan . Suna hangoshi sukayo kan suna wllh koya fito da ƴar Shegiyar daya ɗauka matsayin ƴarsa ,da kwarton ta da suka ajiye agida,ko kuma su kashe shi yanzun nan. Kallonsu yayi cikin kamala da dattako yace "ikon Allah me kuma mukayi dazaku kashemu?wace yarinyar kuke nema?bayan wacce mai gari ya riƙe agurinsa?baffa ya faɗa kai tsaye ba nuna alamun tsoro. Nan wani lawwali yace masa"ai jiya yarinyar nan saida ta bari dare ya raba sannan ta sami lamiɗo tayi masa jina jina,gaba ɗaya ƙafafunsa sun ƙarye,ga hannun damanshi ma ya ɓalle baral, sannan ta gudu,kuma munsan tabbas tana gidan nan,dan kuwa hansai ta kai labari, Kuma ta fayyace mana komai game da yarinyar ,ashe Shegiya ce ka tsinto ka kawo gidanka,sannan ka ajiye mata wani gardin suke lalata dashi,dan haka gaba ɗayanku yau sai hukunci ya hau kanku,dan lamiɗo yana nan banda ihu ba abinda yake yana kiran maciji zai kashe shi,fattu ce tayi masa ture.sannan arɗo ma yana can hannunsa guda ya shanye ya zama kamar sillan kara ,kuma duk aikin fattu ne ,dan haka yau wllh saimun kashe fattu"lawwali ya ƙare zancensa yana mai ɗaga sandarsa sama. "Toh me yasa baku shiga kun duba fattun ba ?idan nan ta dawo,ita wacce ta kai muku rahoton saita faɗa muku inda fattun take"baffa ya faɗa yana ƙoƙarin shigewa gida. "Ƙarya yake wllh, saidai in ya boyesu ,ko kuma sun gudu ,dama naji yana cewa su gudu dan haka karku taga masa " na tsinkayo muryar gwogwgo hansai na faɗin haka ,dan taji mugun haushi da ba'a sami su fattu cikin gidan ba. Aikuwa baffa yana tsaye Ba zato ba tsammani yaji sun rufeshi da duka ta ko ina. Har saida suka kaishi ƙasa.sannan suka taitayeshi sai gurin. Mai gari.suna zuwa suka tarar ana yiwa mai gari ɗori sai ihu yake yana kuka.dan haka can ɗakin hukunci suka jefa baffa,wanda yayi kaishi sosai dan ya daku. Allah Sarki baffa ,Allah ya saka maka. Fattu kuwa tsabar kuka har muryarta ta dashe,can jikin ƙarshen motar ta koma tare da haɗe kai da gwuiwa tana kuka marar sauti ,jikinta sai rawa yake ,fuska ta kumbura suntum tayi jajur ,abinka da farar fata. Abeed yana daga gefe yana kallonta ,sosai yake jin kukanta har cikin ransa,haƙiƙa yarinyar tana fuskantar ƙalubalen rayuwa and she's to Young to handle the situation.amma ya zatayi?dole ta ɗauki ƙaddara yadda yazo mata. Kallonta yayi yadda jikinta ke ta rawa tana shashsheƙar kuka,yaso ace ya iya rarrashi, daya rarrasheta ,koba komai itaɗin yanzu amanarsace,amma Gara tayi kuka ,koba komai zata rage jin raɗaɗin da taleji cikin zuciyarta. Tafiya suke sosai ,Dan drivern gudu yake tsulawa,kasancewar safiya ce hanyar ba motoci sosai,sai jifa-jifa suke cin karo da motocin. Abeed yayi shiru ,tare da jingina kansa jikin kujerar da yake zaune,ba abinda ke yawo cikin zuciyarsa,sai labarin da baffa ya bashi na cewar wai shiɗin amaciji suka ganshi,to ta yaya?yaushe hakan ta faru,me yasameshi? Tabbas idan har abinda baffa ya faɗa gaskiya ne baya raba ɗayan biyu cewar sharrin Amma ne wannan ,dan ita kaɗai yake tunanin zata iya cutar dashi ,tunda afili take nuna masa ƙiyayya, amma zaibi abin ahankali harya gano mugun ƙullinta akansa kafin ya ɗauki mataki. Ya rasa me ya tsareta Amma arayuwa sam bata ƙaunarsa ,kullum burinta ta cutar dashi,tun yana ƙarami yake fuskantar tsangwamarta,har kawo yanzu bata fasa ba ,amma akwai lokacin da ko ance tayi masa wani abun bazata iyaba. Juyowa yayi ya kalli inda fattu ke zaune ,har zuwa wannan lokacin kuka take ,banda rawa ba abinda jikin ta keyi.wani tausayine yaji ya kama zuciyarsa ,wannan kukan yayi yawa zai iya haifar mata da matsala.dan haka ahankali ya ɗan matsa kusa da ita ,ƙureta yayi da ido ,yana son yayi mata magana amma baisan me zaice mata ba. Kusan minti uku yayi yana kallonta da yadda jikinta ke rawa sosai,kafin ya sanya hannunsa ahankali ya dafa kanta . Da sauri fattu ta ɗago kanta agalabaice ,idonta ya mugun kumbura yayi jaaa!sosai lips ɗinta sai sheƙi yake .kallonsa tayi wani sabbin hawayen na kwararowa daga idanunta. Dan yatsansa ya sanya ya share hawayen dake zuba daga idanunta,amma wasu na ƙara zubowa. Da gyar ya buɗe bakinsa cikin hausarsa da bata fita sosai yace "menene"ya faɗa yana kallon cikin idanunta ,gabansa sai bugawa yake,ya rasa mai yasa inhar zai sanya idonsa cikin nata ,to gabansa yayi ta bugawa kenan. Cikin dasashshiyar murya wacce kuka ne yasanya ta dashe fattu tace "Baffana" cikin yanayin shagwaba irin na masu kuka tayi maganar. Wani yummmmmm!!!Adeeb yaji tun daga tsakiyar kansa har babban dan yatsan ƙafarsa.dan yanayin yadda tayi maganar sai yaji wata irin kasala ta kama shi. Ahankali ya kumshe idanunsa yayi jimmm!kafin ya buɗe su ya ɗora akan fattu"is ok ki daina kuka"ya faɗa ahankali yana mai janyowa zuwa jikinsa ,dan shikam hakan kaɗai yake ganin zai yi mata tayi shiru. Allah Sarki fattu kuwa tayi luƙus akan faffaɗan ƙirjinsa sai ajiyar zuciya take sauƙewa,kuma cikin ƙanƙanin lokaci ta fara jin zuciyarta nayi mata sanyi, tana nan kwance ajikinsa barcin wahala yayi gaba da ita. Shikuwa Adeeb gaba ɗaya jinsa yake wani irin,sam ya kasa samun nutsuwa jinta da yayi cikin jikinsa ,gaba ɗaya yaji yanayinsa na sauyawa zuwa kasala da jin wani abu mai kama da feeling ,ahankali ya jingina kansa jikin kujerar ,tare da kumshe idanunsa yana mai ƙara gyara mata kwanciyarta. Tunanin Abie ya fara yi aƙokarinsa na kawar da abinda yake ji acikin jikinsa ,dan aganinsa wannan yarinyar tayi ƙanƙantar da har zai rinƙa jin wani abu akanta,saidai sam jikin nashi yaƙi bashi haɗin kai,dan ji yayi lamarin na ƙara rikice masa,ganin ba sarki sai Allah yasashi cire ta daga jikinsa ya jingina ta da jikin kujerar da suke kai. Ajiyar zuciya ya sauƙe yana mai kallon kyakyakywar fuskarta ,wacce ta ƙara wani jaaa!sosai ,ahankali ya sauƙe idanunsa zuwa lips ɗinta waɗanda ta ɗan turosu Baga cikin shagwaɓa kamar kamar yadda yara keyi idan suna son yin kuka. Haka kawai ya tsinci kansa da sakin wani murmushi mai ƙayatarwa, hannu yasa ya gyara mata hulɗar kanta,wacce ta ɗan zame har gashinta na gaban goshi yasami damar fitowa . Bai ankara ba yaji driver na cewa sun iso Kano,kallon garin yake ,yana tunanin inda zasu sami hotel ,dan su ɗan huta sannan ya sai kaya ya cire wannan na jikin nashi,dan sun matuƙar takura masa. Tambayar drivern yayi nawane kuɗinsa ya faɗa masa ,bashi yayi cikin wanda baffa ya basu da zasu taho, sannan yace wa mai motar dan Allah hotel yake son zuwa . Nan mai motar ya tare musu dan adaidaita yace ya kaisu hotel mafi kusa. Ganin fattu na barci yasa Adeeb bai tashe ta ba kawai ɗauki ta yayi kamar ƴar tsana ya shiga adaidaita ya zauna ,sannan itama ya zaunar da ita.kuma ko buɗe ido batayi ba ,dan barcin sosai ya kamata. Bayan sunje ne ya kama musu ɗaki, sannan ya nufi ɗakin ,har lokacin kuma fattu na rike ahannunsa dan baya don tashi ta daga barci. Da hannu ɗaya yayi amfani wajen bude dakin sannan ya shiga,kwantar da ita yayi akan gadon ya lulluɓawa da ƙarin bargon dake kan gadon,sannan ya ɗan zauna shima yana mai lumshe idonsa ,gaba ɗaya agajiye yake jinsa , dan bai saba irin wannan tafiyar haka ba. Fita yayi ya siyo musu kaya a store ɗin cikin hotel ɗin sannan yayi musu odar abinci ya dawo,fattu nata barci taji laushin gado da katifa ga ƙaton bargo .lol Tashi yayi ya shiga bayi yayi wanka,ya faɗa sosai kafin ya fito,agurguje ya sanya kayan daya siyo ,riga da wando ne na jins da boxers and singlet, sai turare ,sannan yayi sallar asuba. Masha Allah duk da bayani shiri yayi ba ,amma karkuso kuga irin kyan da Adeeb yayi ,sosai ya ƙara zama cikakken Balarabe mai tsananin kyau,sai ƙamshi yake zubawa. Kwankwasa ƙofar dakin akayi, ahankali ya tashi yaje ya buɗe ,abincin da yayi odar ne aka kawo,kaɓar yayi ya dawo ciki. Kallonta yayi yaga bata tashi ba ,dan haka ya zauna yana cin abincinsa.kaɗan yaci ya tashi ,da alama bashi da yawan cin abinci sosai. Gadon da fattu ke kwance ya nufa ,ahankali ya ɗan yaye bargon daya rufa mata,hannunsa yasanya saman goshinta,har lokacin jikinta da zafi sosai. Filin da take kai ya ɗan bubbuga sau uku, ahankali ta buɗe idonta tana mai turo baki ,sai kuma tayi saurin tashi tana ƙarewa ɗakin kallo ,wai aljanar duniya nan ɗin shine gidansu hamma Adeeb ?lallai yan gayune su,ji laushin gado kamar auduga.fattu ta faɗa cikin zuciyarta tana mai ƙarewa dakin kallo. Ji dan Allah yadda take ta wani kallon daki kamar bata taɓa ganin daki ba "Adeeb ya faɗa cikin zuciyarsa yana ɗan kallonta. "Go and get your shower" Adeeb ya faɗa ahankali yana mai kawar da kansa . Kallonsa take ƙuri tana rarraba ido,dan bata fahimci me yake cewa ba. Jin bata tashiba yasa shi dan juyowa yana kallonta. "Ɗan harararta yayi kafin yace " nace kije kiyi wanka ne"ya faɗa fuskarsa aɗaure ba walwala. Tashi fattu tayi sumi-sumi ta nufi hanyar fita ,tana zuwa bakin ƙifar taja ta tsaya tare da juyowa yana kallonsa. Shima kallonta yake cike da jin haushi ko ina zata kuma?nace take tayi wanka. Ganin irin kallon da yake mata ne yasa tace "bazan iya budewa ba"ahankali tayi maganar cikin dasashshiyar muryarta kanta aƙasa. Harararta yayi cike da jin haushin wai yaje bakin ƙofar fita, kuma tana faɗin bazata iya buɗewa,sai kace nan ne toilet ɗin. Tashi yayi ya nufi bakin ƙofar toilet ɗin ya buɗe sannan ya juyo yana kallonta. Shiru tayi itama tana ɗan kallon nasa,dan bata gane nufinsa ba. Wata iska ya furzar mai zafi yana lunshe idonsa,kafin yace "zo kishiga "ya faɗa yana kallonta ,fuskarsa sam ba walwala,shi wllh ya gaji da wannan shirmen nata fa. Kanta adurƙushe tazo ta shige toilet ɗin , kayan daya siyo mata ya ɗauki tare da ɗan kwankwasa toilet ɗin ya buɗe kadan yace "take" Fattu kuwa da tun shigar ta toilet ɗin ta saki baki galala tana kallon ikon Allah,anya kuwa yasan inda ya buɗe mata yace tazo tayi wanka?yo wannan ai Dakin kwanan ne,kalli da harda wani ƙaton gado mai rami,to ma ta a ina zataga ruwan bare har tayi wankan? Juyowa tayi tana kallon farin hannunsa daya miƙo mata leda.ƙarasawa tayi kusa dashi ta karɓi ledar sannan tayi saurin cewa "inane banɗakin? "What " ya faɗa yana mai buɗe kofar gaba ɗaya ,sannan ya kalli fattun ko fara wankan ma batayi ba. Cikin faɗa -faɗa yace "do you expect me to West my time here?Ina jiranki?"ya faɗa yana zaro mata manyan fararen dara-daran idanunsa. Nan da nan jikin fattu ya kama rawa ,tsoro ya kamata ,har kayan hannunsa saida suka faɗi ƙasa" duk da batasan me yake cewa ba ,tabbas ta san faɗane yake mata ,cikin muryar kuka tace"dan Allah hamma kayi haƙuri bansan a inda zabga ruwan ba"ta faɗa tare da fashewa da kuka tana mai toshe bakinta. Shiru yayi yana kallonsa,lokaci guda kuma tausayi ta ya kamashi, sai yanzu ya tuna daga inda ya taho da ita,ba abin mamaki bane idan tace bata san ya zata yi ba.dan haka cikin sanyin murya yace "is ok daina kuka "ya fadi yana mai ƙarara shigowa toilet ɗin. Idan kina son yin wanka nan zaki danna ruwa zai zubo, sannan idan kina biyan buƙata nan zaki zauna ,In kin gama saiki dannan nan ,wannan na wanke bakine and ga soso da soap kin gane "ya faɗa yana kallonta . Kai ta ɗaga masa alamun ta gane , Hanyar waje ya nufa sannan ya juyo yace mata "kiyi sauri yanzu zamu wuce"yana faɗin haka yayi waje. Zama yayi abakin gadon yana mai dafe kansa,ciwo yaji kansa nayi , sakamakon wannan doguwar maganar da yayi, gaskiya kula da yara akwai wahala ,ji yadda tasa masa ciwon kai rana ɗaya kawai. Fattu kuwa bayan ta cire kayanta na gado ,wato rigar fulaninta ƴar dingila da zanin ta ,kai tsaye gurin soso da sabulun nan ta nufa ta ɗauka sanna tazo ta tsaya saitin gurin da akace idan ta danna ruwa zai zo ,dannawa tayi tana jiran taga ta ina ruwan zai zubo,ai ba zato ba tsammani kawai taji ruwa akanta shaaaaaa!!! Wata zabura da fattu tayi tare da watsar da soso da sabulun nan ta kurma uban ihu iya ƙarfinta ta nufi kofar fita ba komai ajikinta "wayyo Allah na hamma wayyo kazo ka buɗe ni na shiga uku dakin yan shan jini ka kawoni ana min ruwan jini akaina wayyo hamma am" abinda fattu ke faɗa kenan cikin rikicewar da tashin hankali gaba ɗaya jikinta rawa yake kamar ɗan mazari. Adeeb na kwance a gefen gado yayi nisa cikin tunani kawai ya biyo ihunta ,ai baisan lokacin daya zabura da mugun sauri yayi toilet ɗin ba,yana zuwa ya buɗe kofar da da sauri ya danna kansa ciki. Kicibis sukayi da fattu abakin ƙofar, tayo gunsa ga gudu tana kuka. Wani irin bugawa ƙirjin Adeeb yayi kansa ya hau juyawa ,sakamakon ganin da yayiwa fattu haka zirr ɗin ta ba kaya.tunda yake arayuwarsa yau ya taɓa ganin mace data fara girma haka ba kaya agabansa. Cikin hanzari ya juya bayansa yana mai dafe ƙirjinsa dake barazanar fashewa."innalillahi "ya faɗa cikin sassarfa lokacin dayaji fattu ta kankameshi tana kuka. "Sosai shima jikinsa ya hau rawa kamar ɗan mazari,cikin rawar murya yake faɗin"le..a...ve. me... Lea....ve... M....e" yana kasa nutsuwa yayi mata magana. Fattu kuwa banda rawa ba abinda jikinta keyi,wannan wace irin masifa ce haka?wane irin gida ya kawota ,za'a cinyeta ya sama. Runtse idanun Adeeb. Yayi da mugun ƙarfi yana ambaton sunan Allah ,ya ɗauki kusan minti biyu cikin halin ruɗewa da rawar jiki.gaba ɗaya jikinsa yayi wani iri,kafin yayi ƙarfin halin sanya hannunsa dake rawa ya fizgota daga bayansa tare da tureta can gefe guda,yana mai sauƙe numfashi cikin sauri ,kawar da kansa yayi daga gareta yana mai cewa"kisa zani ki rufe jikinki Please. Fattu kuwa cikin rawar jiki ta ƙara matsowa gareshi sam tama manta da batun wasu kaya,"dan Allah ka fitar dani daga ,Ni gurin baffana zani "ta faɗa cikin kuka. "Kisa zani nace miki"ya daka mata tsawar data ƙara hargitsata.tsugunnawa tayi tare da ƙanƙame jikinta tana kuka. "Ni ka kaink gurin baffana dan Allah ka maidani gurin baffa "abinda take daɗi kenan cikin kuka da rawar jiki ,gaba ɗaya ta gama tsorata . Zanin nata Adeeb yaje ya yayumo cikin lalube,dan ko gani batayi sosai .yana zuwa ya lulluɓa mata sannan,ya fice daga bayin, da gyar ya iya ƙarasawa kan gadon yana zuwa ya faɗa kan gadon tare da duƙunƙune jikinsa yana rawar sanyi ...... Masu karatu mutara next oage. Ina ganin comments ɗinku masoya ta ko ina ,ina matukar jin daɗi da ƙaunarku ga wannan novel ɗin . Na gode sosai Allah ya bar ƙauna , And I love you guys where ever you are🥰🥰🥰🥰 Anty mammy ce Mrs babi💘💘 [7/17, 7:11 PM] Abue Saleh AlQuyraemey: 🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄 MACIJI NE 🪱🪱🪱 Na mammy kabeer (Anty mammy) Elegant online writers📚📚 Free book Page 23/24 _________________Kwanci Adeeb yayi akan gadon ,tare da duƙunƙunewa guri ɗaya ,jikinsa kuwa banda rawa ba abinda yake ,idanunsa arufe ruf! Ba abinda yake gani cikin idanunsa face hoton surar fattu. "Ya Salam ! Ya Allah save"Adeeb ya faɗa ahankali yana mai riƙe matarsa data ke masa wani ciwo na lokaci guda. Fattu kuwa tana jin fitarsa da sauri itama ta fito tana kuka.jikin madubi taje ta tsaya tana kallon yadda ya faɗa kan gadon tare da dunƙulewa yana rawar sanyi,cikin ranta take rayawa kodai baida lafiya ne ?ko shima zazzaɓin yake ? Ganin idan ta tsaya zancen zuci saita shekarar agurin,gashi batayi sallaba. Dan haka cikin tsoro da fargaba ta fara takawa zuwa jikin gadon ,tana zuwa taka ta tsaya ,tare da sanya bayan hannunta ta share hawayen daya silalo daga cikin idanunta. Cikin sanyin murya tace "hamma zanyi sallah" ta faɗa kanta a ƙasa. Yana jinta yayi shiru abinsa, yana ci gaba da jin yadda matarsa ke masa ciwo tana ƙullewa,ahankali yake karanta addu'oi cikin ransa ,fatansa kawai ya daina jin wannan azabar da kuma yanayin dake bibiyar ilahirin jikinsa. Kusan minti biyar fattu na tsaye kanta aƙasa ,jifa jifa tana share hawayen dake zubowa daga idanunta.aranta kuwa cewa take "wannan hamma wllh baida kirki ,san ba bakinsu ɗaya da macijina ba,dubi yadda nayi masa magana ya wani shareni. Shikuwa Adeeb yana kwancene yana ci gaba da ambaton sunan Allah,harya samu marar ta kafa masa ,sai wani uban gini dake karo masa agishinsa ,duk da sanyin a.c dake ɗakin hotel ɗin. Ahankali yake sauƙe ajiyar zuciya yana ɗan kumshe idanunsa.kafin ya tashi zaune yana mai dafe da kansa. Ganin ya tashi zaune yasa Fattu ɗan ja da baya,dan ita tsoronsa ma takeji yanzu ,dan wllh da gani masifaffene. Kallon gefen ta yayi ba tare da ya lalle ta kai tsaye ba,sannan ya ɗan ja tsaki yana mai yamutsa fuska da turo baki,kamar wani mace ,sannan ya miƙe ya shiga bayin ,ruwan wanka ya haɗa mata cikin boket dan yasan ba iya shiga kwamin wannan zata yi ba, sannan ya ɗauki sisi da sabulu ta ajiye mata .ya ratsa makilin acikin sabon burush sannan ya ɗan leƙa cikin ɗakin .tana tsaye kamar gunki ,har lokacin share hawaye take ,kumshe ido yayi yana mai cewa, wannan ta cika kuka ,cikin ransa. Kafin ya buɗe baki ahankali yace "zo" ya faɗa kamar baya so.badan Allah yasa Fattu mai saurin ji bace da bazata ji me yace ba. Ahankali take takowa cikin yanayi na tsoro,dan dai tana tsoron masifarsa ne da ba abinda zai sa ta koma wannan ɗakin da ake ruwan jini. Shiga tayi tare da tsayawa tana kallonsa.jikin sink ya matsa tare da miƙa mata burush ɗin yana mai cewa "oya wash your mouth" Shiru fattu tayi tana kallonsa tare da kallon burush ɗin data karɓa daga hannunsa. Kallon ta yayi shima fuska aɗaure yace "wanke baki" ya faɗa cikin ƙosawa ,yana jinjina ƙauyanci irin na fattu wai ko burush bata sani ba. Ita kuwa fattu kallonsa tayi tare da kallon burush ɗin ,cikin ranta tace ikon Allah ,su nan da wannan abun suke wanke baki,mutuwa saidai hawaye da gishiri.ƙara kallonsa tayi suka haɗa ido,da sauri kowa ya kawar da kansa ,cikin shagwabar da fattu batasan tana da ita ba tace "hamma Ni ban iya wanke baki da wannan ba"ta faɗa tana miƙa masa burush ɗin. Wani yarrrrr yaji ajikinsa, saboda salon yadda tayi maganar ,saiyaga kamar da gangan take wani abun.harara ya salla mata kafin ya karɓi burush ɗin yace "open your mouth" Gurun fattu tayi tana kallonsa ba tare da ta buɗe bakin ba. Runtse ido yayi cikin ciwon rai yace da ɗan ƙarfi"haaaaaa"ya faɗa yana bude dan madaidaicin bakinsa. Buɗe nata bakin tayi kamar yadda taga yayi, wanda yake nan ɗan mitsitsi kamar gidan tsutsa ,haƙora ta farare tass dasu,ajere reras. "Masha Allah "Adeeb ya faɗa cikin rashin sanin ya furta hakan. Saida ya faɗa kafin ya ankare.kallon fattu yayi suka haɗa ido,harara ya watsa mata yana mai cewa"kaki cinyeni da wannan lulu eyes ɗin naki"Adeeb ya faɗa yana mai sanya burush ɗin cikin bakin fattu. Ahankali yake wanke mata haƙoran nata masu kyau da ɗaukar hankali,yana wanke wa yana kallon fuskarta,ita kuwa ta rufe idanunta ƙam!wani irin takeji bakin nata,gashi abun da shegen zaƙi, anya kuwa ba abin sha bane ya manta yace na wanke baki ne? Aikuwa wllh saita ɗan sha taji ya faɗinsa yake.Adeeb bai sankara ba kawai yaga ta tattara kumar bakinta ta haɗeye ƙut! Zaro ido yayi tare da buɗe baki cike da mamaki yace "what!!" Kin shanye kunfar?oh my God" ya faɗa yana zare burush ɗin daga bakinta. Yace "oya fito dashi"ya faɗa yana zare mata idanu. Shagwabar fuska fattu tayi kafin tace "ai na shanye zaƙi gareshi" ta faɗa tana mai sunkuyar da kanta. Girgiza kai kawai Adeeb yayi,baice komai ba ya kunna fanfo yace ta tara ta kuskure bakin, Hannu ta saka ta tari ruwan sannan ta kuskure bakinta.wani fayau taji bakin nata yayi ,sosai taji yayi mata daɗi ga kamshin strowberry da bakin keyi. Nuna mata ruwan wanka yayi yace tayi wanka ,yanzu ta fito yana jiranta. Kai ta daga masa,tana nufar gurin da boket ɗin yake ajiye. Harya kama handle ɗin kofar sai kuma ya juyo yace "kiyi alwala anan"ya faɗa yana nuna mata jikin sink din tare da ficewa. Zama yayi abakin gado bayan fito daga toilet ɗin ,haka kawai yaji yana cikin farin ciki,sai murmushin yake,abinda ba al'adar shi bace yawan fara'a. Fattu kuwa ko minti biyar batayi ba ,sai gata ta fito sanye da Kayan ta data cire . Kallon ta Adeeb yayi yace " ina kayan dana baki?" Miƙa masa al'adar tayi tana mai cewa"bazan iya sawa ba harɗe Ni zasu yi" Kallon ledar yayi sannan ya lalle ta, karba yayi tare da budewa ya zazzage,doguwar rigar baƙa mai dan faɗi sai ɗan kwalin rigar shima baki,kuma yana da girma.wai amma sune bazata iya sawa ba ' "Take it ,ya faɗa cikin hade fuska. Kallonsa tayi, tare da karɓar ledar,bawai dan ta ji me yace ba ,saidan taga yana miƙa mata ledar . "Wuce kije kisa"ya faɗa ba alamun wasa afuskarsa. Juyawa tayi sumi"sumi ta koma toilet ɗin ,amma bata rufe ƙofarba ,ta yadda dataji burum,zata arce. Haka ta cire kayanta ta sanya wanna doguwar rigar ,masha Allah rigar tayi mata kyau sosai ,saita fito ras da ita.maimaiko ta lulluɓa dan kwalin ,sai kawai ta daura akanta.,sannan ta sanya kayanta wanda ta cire cikin ledar sabon kayan. Fitowa tayi tana tattare rigar ,dan harga Allah jinta take aharharde,tafi don tsangalallen ,zaninta. Tana fitowa Adeeb yabi ta da kallon,aransa yana mai yaba irin Khan da tayi ,amma jibi yadda yake wani dage rigar. "Hamma a ina zanyi sallar?ta faɗa tana kallon gefensa. Shiru yayi yana kallon ta kafin yace "zo nan" Cikin tsoro take takowa har zuwa kusa dashi,tana fatan kar yayi mata faɗa irin na ɗazu. Mikewa yayi tare da zare ɗan kwalin kanta,ya warware shi tare da yi mata rolling irin yadda yaga amminsa da ƙannansa nayi. Masha Allah ai nan danna fattu ta fito abalarabiya sak, tayi kyau sosai da sosai,kamar ba fattu yar fillo ba. "Kije can kiyi sallah"ya faɗa yana nuna mata kan dardumar da yayi Sallah shima. Bayan ta idar da sallar Adeeb yana kallon ta,masha Allah ba wani kuskure cikin sallar Tata,dan fattu tana da ilimin addini sosai. Abinci ya nuna mata yace tayi sauri taci zasu tafi.bata wani ciabincin kirki ba,dan ji tayi sam abincin baiyi mata daɗi ba,tafi son tuwo ko madarar shanu. Shima bai wani damu ba ,dan yaga bataci abinci ba sosai.tashi yayi yace mata suje . Yayi gaba tana binsa abaya. Riƙe da rigarta, hannun dayan kuma tana riƙe da ledar kayanta. Suna fita daga hotel ɗin kai tsaye gurin masu saida waya ya nufa , wata ƙaramar waya ya siya da layi,ba tare da ya tambayi kuɗi su ba ,naga ya bada duka kuɗin nan dake cikin leda,dan dama suna hannunsa,wanan rigar kawai ya cire daga ledar,sosai naga mai saida wayoyin yana ta murna da godiya har kasa ya durƙusa yana godiya. Haɗa wayar Adeeb yayi tare da sanya layin ,kati ya karɓa gurin mai saida wayar ,aikuwa da sauri ya ɗauki mata na dari biyar ya mika masa. Wata number naga ya daddana cikin wayar,bayan ya gama sanya katin acikin wayar. Magana ya farayi cikin harshen larabci,bayan anɗaga wayar daya kira.ni dai ba dan me yake cewa a,saidai naga kamar yana kwatancen inda yake ne. Bayan ya kammala wayar ne yana ƙoƙarin sanyata cikin Aljihu,kawai yaji mutum yana ƙwaƙwumarsa kamar za'a shige cikin jikinsa. Da sauri ya kalli gefen hagunsa ,inda tanan yake jin alamun mutum ɗin,aikuwa fattu ya gani tsaye ta kama gefen rigarsa,jikinsa har rawa yake tana ɓoye fuskarta ajikinsa. Hannunsa ya sanya tare da kamo hannunta ya dawo da ita zuwa gabansa. Saida ya ɗan harareta kafin yace "menene kuma"ya faɗa cikin salon maganarsa kamar baya so. Ahankali fattu ta nuna masa wasu matasa kusan su goma da suka tsaya suna kallonsu.tace "waɗan can ne ke kallona "kallon gurin matasan yayi,yaga yadda suka kafesu da idanu,kuma ba akowa suke kallo ba face fattu,nan da nan yaji wani irin ɓaci rai da ciwon zuciya ya turnuƙeshi, Cikin hanzari ya maida fattu bayansa yana mai hararar matasan nan,zuciyarsa kamar zata fito dan tsabar ɓaci rai.gaba ɗaya yaji gurin yayi masa baƙi kirin,Bama yason tsayuwa agurin, dan haka cikin zafin nama ya fizgi hannun fattu suka fara tafiya daga gurin,mai saida wayoyin yana ta masa godiya da Allah ya kiyaye amma ko sauraransa baiyi ba. Can wani guri ya koma tare da tsayawa ,shi kaɗai dai huci yake,dan me zasu tsaya suna kallon ta ,shifa saiyaga kamar ma ɗaya ƙirjin fattu yake kallo. Cikin sauri ya juyo tare da kallon fattu tun daga sama har ƙasa.ba wani abu daya bayyana ajikinta ,wanda za'ace shigarta batayi daidai ba ,saidai fa idan ka ƙura mata ido zaka iya gane ba bra ajikinta. Lallai ke nan bata sanya bra ajikinta? "Ke meyasa baki saka wannan abun ba kafin kisa rigarnan" Ya faɗa cikin fushi da bakin rai. Kallonsa fattu tayi cikin rashin fahimta dan bata gane me yake nufi ba,kawai saita sunkuyar da kanta ƙasa tace "kayi haƙuri Ni banga komaiba inda rigar ba"ta faɗa Muryar har ta fara rawa,alamun zata yi kuka. Harya buɗe baki zaiyi magana yaji wayarsa na ringing,tsaki yayi kafin ya ɗaya call ɗin. Shiru yayi na tsawon lokaci kafin yace "Yes i sawa them"ya kashe wayar . Dan fitowa yayi daga gurin dasuke tsayen naga ya ɗaga hannunsa . Wata tsuleliyar mota naga ta taho gareshi,suuuuuu,baka ko jin ƙagarta,kallon ɗaya zakayiwa motar kasan anɓadda Naira agurin,farking motar tayi agabansa,kafin mai riƙon ya fito cikin sauri yana mai faɗin "your highly well come back sir"mutumin ya faɗa yana mai durƙusawa har kasa gaban Abeed. Kafadar mutumin Abeed ya dafa tare da miƙar dashi tsaye,sannan ya ɗan rungumeshi yana mai bubbuga bayansa. "Let go hisham"Abeed ya faɗa yana mai nufar motar ,da sauri wanda aka kira da Hisham ya budewa Adeeb motar ,shikuma ya shiga gidan baya ya zauna. "Hamma " fattu ta faɗa cikin sauri tana mai ƙarasowa jikin motar ganin ya shige cikin motar yana ƙoƙarin barcinta. Adeeb kuwa da gangan yayi banza da ita ,intaga dama ta ƙara so ta shiga motar,dan haushinta ya keji sosai ,ai da gangan ta wani tsaya har wasu ba zaune ke ƙare mata kallo. Hisham ne ya kalli fattu yace "yan mata lafiya kuwa? Shagwabe fuska fattu tayi tana kallon Adeeb tace "gurin hamma zani gashinan acikin nan"ta faɗa tana nuna mai Adeeb ,wanda ya wani ɗauke kai . "Yallaɓai this ... "Let her in"Adeeb ya faɗa cikin katse Hisham . "Yes sir"Hisham ya faɗa cikin bin umarni,ya kauce daga bakin ƙofar motar yana mai cewa fattu"shiga" Da saurinta kuwa ta shige kusa da Adeeb ta zauna ,harda sauƙe ajiyar zuciya. Ahankali ta sanya hannunta tare da riƙe gefen rigar Adeeb ta kalle- kallen motar.banda faɗuwa ba abinda gabanta keyi. "Yallaɓai where are we going now" Hisham ya tambaya cikin girmamawa. "Abuja" Adeeb ya faɗa tare da kwantar da kansa jikin kujera ,ac na ratsa shi ta ko ina. Nan Hisham ya kunna mota suka cilla sai Abuja. Ko daga Abuja kuma sai ina ? Ga dai Hajiya fattu cikin mota mai a.c ana baza idanu. Muje zuwa ku biyoni sannu kan hankali. Anty mammy ce Mrs babi💘💘💘 [7/18, 9:07 PM] Abue Saleh AlQuyraemey: 🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄 MICIJI NE 🪱🪱🪱 Na mammy kabeer (Anty mammy) Elegant online writers📚📚 Free book Page 25/26 ________________Tafiya suke cikin motar Ba tare da kowa ya ƙara cewa komai ba,ba abinda ke tashi cikin motar dai sanyi a.c da daddaɗan kamshi, gefe guda kuma ƙira'ar sudais ke tashi cikin suratul mulk. Gaba daya zuciyoyinsu,sun sami nutsuwa,irin wacce mai sauraron Alƙur'ani ke samun tago mashi da ita. Adeeb yana kwance cikin kujerar, idanunsa alumshe ,ahankali yake ɗan motsa bakinsa yana bin ƙira'ar,al'adar sa kenan dama shi,inda yana cikin mota ,to karatun alƙur'ani yake sauraro. Yayin da can ƙarƙashin zuciyarsa yake jin wani irin farin ciki da annashuwa,duk da baisan tsawon lokacin daya ɗauka cikin yanayi na wata halittar ba,amma yana ji ajikinsa cewa yayi kewar ahalinsa fiye da yadda yake tunani.ba abinda yake fata da buri irin ace yaganshi kusa da abie da ammi.ko wane yanayi zasu shiga idan suka ganshi? Tunanin da Adeeb yayi tayi kenan cikin zuciyarsa.hakan ya hana masa fahimtar halin da fattu ke ciki.wato ta takure jikinsa sosai,sai rawar sanyi takeyi, sosai sanyin motar ke damunta, ga wani irin yanayi na kewar baffanta dake taso mata, sosai ta ƙunaci Jikin Adeeb ,aƙoƙarinta na samun gurin da dataji ɗumi. Ahankali ta ɗan zakuɗa kadan zuwa jikinsa,ta yadda har kafaɗarta na gugar tasa.kuma har zuwa wannan lokacin tana riƙe da gefen rigarsa. Shikuwa Adeeb jin anɗan bugeshi ,yasa shi buɗe idanunsa ahankali, ɗan juyowa yayi yana kallon fattu, wacce tayi lugus ajikinsa tana karkarwa. "Ke matsa daga jikina"ya faɗa cikin salon maganarsa ba tare da ya motsaba. Da sauri fattu ta ɗan matsa ,daga jikin nashi,dan ita atunaninta dama yayi barcine. Kallonsa tayi tare da marairaicewa tace "Hamma sanyi nake ji,kodai cikin ƙanƙara muke tafiya"ta faɗa zuciyarta ɗaya,tana ɗan gwabe fuska. Kallonta yayi tare da harararta yace "dake baki san acikin ƙanƙara muke tafiyaba?ya faɗa cikin gatse. Zato ido fattu tayi tare da dafe ƙirji,"na shiga ukuna Ni fattu ,dan Allah Hamma kayi min rai,mu canja wata hanyar wllh mutuwa zanyi idan naci gaba da jin sanyin nan"fattu ta faɗa cikin marairaita tana rawar sanyi,gaba ɗaya ta gama tsorata,idanunsa kuwa harya fara kawo ruwa. Bamza Adeeb yayi da ita tare da maida idonsa ya rufe,wannan gaskiya ɓaci ƙauyencima akwai shirye atattare da ita,kamar ba tare suka shiga motar ba, ko ina taga alamun ƙanƙarama bare tace akanta suke tafiya? Fattu kuwa ganin ya maida idanunsa ya rufe sai tsoro ya ƙara makata,da sauri ta cusa kanta tsakanin hannunsa da kujera, ta kara ƙanƙame gefen rigarsa tana kuka. "Wayyo Hamma sanyi nakeji yana shiga cikin ƙashina ,jinina daskarewa yake" fattu ta faɗa cikin kuka,tsakaninta da Allah take kukanta. Dafe kai Adeeb yayi tare da kallon Hisham yace "switch up that a.c" ya faɗa kamar baya so. "Ok sir" Hisham ya amsa tare da kashe a.cn yana mamaki,yau yallaɓai ne da kansa yace akashe a.c? Fattu kuwa ahankali taji ta daina jin sanyi da take ji,dan haka share hawayenta tayi tana mai cewa aranta."anya kuwa Hamma ba so yake ya kaini gurin yan shan jini su tsotsemin jini ba? Ahankali ta dago kanta tana kallon fuskarsa ,shagala fattu tayi da kallon kyakyakywar fuskarsa ,barin ma light pink lips ɗinsa da gashin baki yayi masa ƙawayan,ga gemunsa mai kyau sai sheƙi yake,hanci kuwa kamar wanda aka ɗora masa,gaskiya Hamma akwai kyau ,inama nike da kyansa,aikuwa danasha gayu. "Ke meye kika ƙuramin ido haka?karki cinyeni" Adeeb ya faɗa yana mai tsare fattu da idanunsa masu tsananin haske. Dan duk yadda ta ƙuresa da ido yana kallonta ,dan ba duka ya rufe idon nashi ba . Ɗan zabura fattu tayi ta matsa baya tana soso kai,dan ba ƙaramin kunya taji ba,ashe yana kallonta ta ƙuresa da ido haka? wayyo Allah Ni fattu .ta faɗa cikin ranta tana mai kwantar da kanta jikin kujera cikin kunya. Tun daga lokacin ba wanda ya ƙarayin magana a cikinsu. Adeeb yana cikin tunaninsa yaji fattu ta langaɓo kansa,dan dubawa yayi saiyaga ashe ma barci tayi.kafeta yayi da idanuwansa yana kallon zallar kyau irin na fattu,duk da ƙarancin shekarunta ,amma Allah yayi mata baiwar kyau,irin kyanda sai kana kallon mutum kake ƙara ganin kyan nashi . Gyara mata kwanciyar yayi agefen kafaɗarsa ,duk da yadda yake jinsa atakure,kasancewar kusancinsu yayi yawa ,amma haka ya daure ya barta akan kafaɗar tashi taci gaba da barcinta. Fattu na cikin barci taji ana dan taffing kumatunta, Ahankali ta buɗe idanunta da sukayi mata nauyi saboda barci. "Dagani malam duk cin batani da yawun barci ko" Adeeb ya faɗa yana hararar fattu Wacce ke kif-kifta idanunta tana mai daga masa kafaɗa,kallon kafaɗar tashi tayi,amma ita bata wani ga yawu agurin ba. Suna fita daga Motar fattu ta gansu kusa da wani ƙaton jet ,Aida sauri ta kamo hannun Adeeb ta rike ƙam cikin nata tana mai zaro ido. Fizge hannunsa Adeeb yayi yana hararar fattu "stop touching please" ya faɗa yanayin gaba binsa. Da sauri fattu ta mara masa baya,tana binsa ƙafa ƙafa.tab yaushe zata tsaya kusa da wannan abu mai kama da girman duniya?haka kawai ya fado kanta ta mutu ? Wani farin Balarabe ne ya fito daga cikin wata ƙofa,dake ɗan nesa da inda jet ɗin ke tsaye. Da gudu naga ya taho ya ruƙunƙume Adeeb yana sunbatarsa,kuma yana hawaye. "Habeebi ina ka shiga ?me yasameka?kasan irin tashin hankalin da muka shiga?kowa na gida yana cikin damuwa,abie yana nan akwance ba lafiya tunda aka rasaka"Balarabe ya faɗa cikin harshen larabci. Murmushi kawai Adeeb yayi yana mai shafa kan wannan balaraben ,sannan yace " where is the imam? Cikin share hawaye mutum yace "yana ciki kai kawai muke jira. Kallon fattu Adeeb yayi yace "jirani ana karki biyoni" ya faɗa cikin hade fuska.kafin yayi gaba. Da sauri fattu ta kamo hannunsa cikin marairaita tace "tsoro nakeji Hamma dan Allah karka gudu ka barni"ta faɗa cikin kwabe fuska. Zare hannunsa kawai yayi baice komai ba suka shige cikin dakin da wanann balaraben ya fito. Zama fattu tayi akan wata kujera dake gefen ta,da alama kujerar sassaƙata akayi dan zama agurin,tagumi tayi rungume da yan kayanta,tunani take yanzu idan Adeeb ya gudu ya barta anan yazatayi? Gurin wa zata?dan ita dai yadda take ganin garin nan da zungura- zunguran gidajen dake cikin garin ,zaiyo wahala idan ba shan jini akeyicikin gidajen ba.shikenan ba ita ba ƙara ganin baffanta. Daga kanta tayi ta kalli inda aka daka motar da suka zo cikinta amma watan bataga motar ba,saidai taga wasu tarin motocin can gefe guda arufe da wani abu. Ƙila duk waɗanda aka kawo su cikin motocin can an shanye musu jininsu.yanzu itama haka za'a shanye nata jinin idan Hamma ya gudu?"wayyo ni fattu naga rayuwa "ta faɗa tana mai leave fuska da waige waige . Shikuwa Adeeb koda suka shiga ƙofar nan, Kusan minti talatin suka ɗauka cikin dakin kafin suka fito, ,lokacin fattu hatta fara kuka, tana ganinsa taji wani sanyi cikin ranta,da hanzarin ta ta miƙa tare da nufarsa tana kuka,tana zuwa ta kama hannunsa cikin kuka take cewa"Hamma harba fara kuka ,nayi tunanin gudawa kayi ka barni, anan ado a shanye min jinina, dan Allah Hamma karka ƙara tafiya ka barni" fattu ta faɗa tana mai ɗora kanta akan damtsen hannunsa. Wani irin yanayi na tausayinsa Adeeb yaji yana ratsa zuciyarsa,Allah Sarki,yasan ahalin yanzu bata da wani gata saina Allah saikuma shi,shi kaɗai ta sani,zaiyo iyakar ƙoƙarin sa ,wajen kula da ita har su cimma burin su. hannunta kawai Adeeb ya kama , tare da nufar cikin jirgin nan. Noƙewa fattu ta farayi cikin rawar jiki tace"Hamma na tuba Dan Allah karka sani cikin wannan abun mai kama da kifi" fattu ta faɗa tana mai ƙoƙarin zare hannunta daga cikin nashi. Tsayawa yayi tare da kallon wannan balaraben yace tareeƙ ka shiga ciki "ya faɗa cikin harshen larabci. Jinjina kai tareeƙ yayi tare da kama ɗayan hannun Adeeb ya sunbata kafin ya shige cikin jet ɗin. Kallonta Adeeb yayi yaga yadda gaba ɗaya ta firgice,sai ƙoƙarin zame hannunta take cikin nashi. Ahankali ya sanya hannunsa ya kawota jikinsa,yayi mata side hug,kana yace " ki nutsu kinji,ba abinda zai miki zamu tafi gidane acikinsa" ya faɗa yana mai shafa kanta. Jinjina kai fattu tayi tare da cewa"Ni bazan bikaba Hamma kamaida Ni gurin baffa ,bazan shiga wannan abunba tsoro nakeji,kifine da,muna shiga haɗiyemu zaiyi Hamma"ta kai ƙarshen maganarta cikin kuka. Murmushin Adeeb yayi akaro na farko tun tasowarsu daga Kano,wai haɗiyesu zaiyi ,kifine.kai wannan yarinyar akwai ƙauyanci. Ganin dai da gaske fattu atsorace take, sai kawai ya juyo da ita zuwa gabansa ,bai jira komai ba ya haɗar da jikinsa ya rungumeta cikin faffaɗan ƙirjinsa,ahankali yake shafa kanta zuwa kafadunta . Shiru fattu tayi sakamakon wani irin nutsuwa mai cike da sa annashuwa dataji tana ratsa dukkan sassan jikinta,luɓ tayi cikin jikinsa ta daina wannan rawar jikin,idanunta kawai ta kumshe tana shaƙar daddaɗan kamshi da Adeeb keyi. Kusan minti uku Adeeb ya bata ajikinsa,yayinda shima yake jinsa cikin wani irin yanayi na samun nutsuwa da peace of mine ,ji yake kamar suyi ta zama ahakan, amma tunowa da yayi da abinda ke gabansa yasashi saurin ɗagota daga jikin nashi,ƙara komawa fattu tayi ta kwantar da kanta akan ƙirjinsa,ba tare da tasan tayi hakan ba,.cibiya ya karatu kafin yace "to dagamin jiki karki karyani"ya faɗa daidai saitin kunne ta. Wani yuuuuuuu fattu taji ,jiri na neman dibanta, lokacin da iskar bakin Adeeb ta bugi kunnenta,da sauri ta rike damtsensa tana mai runtse idanunta,saida suka sake ɗiban minti kusan biyu,kafin Adeeb ya ɗagota,wanna karon bayi musu ba,saidai kanta na ƙasa cikin jin kunya. "Ya isheki haka ko kina don daɗi?"Adeeb ya faɗa yana kallon fuskarta. Shiru tayi kanta a ƙasa ba tace komai ba. Hannunta Adeeb ya kama suka fara taka matakalar. Taku ɗaya biyu kawai fattu tayi luuuuuu zata daɗi ƙasa ,da sauri cikin azama Adeeb ya ruƙota ,yana mai zato idanu waje. Fattu kuwa ji tayi kanta yana juyawa sosai,tace "Hamma ka rikeni zan faɗi "ta faɗa tana mai kumshe idanunta. "Ina tare dake ba abinda zai sameki"Adeeb ya faɗa ,yana mai ɗaya fattu kamar ya ɗauki jaririya ya shige cikin jet din. Wow wato shi kansa cikin jet ɗin abin kallo e ,tsayawa fasalta yadda ya tsaru kuma bata lokacine,na barku kawai ku ƙiyasta tsaruwar jet ɗin. Sin yanufa ya zauna tare da rungume fattu cikin jikinsa,yana shafa kanta ahankali. Belt ya ɗaura musu kafin ya ɗanan wani ɗan guri saiga kujerar ta mike ,yadda mutum zai iya kwanciya akai. Wata har danja ya latsa ,nan danan mai tuƙin wato tareeƙ ya tada jirgin sukayi kula sukayi sama. Ƙara gyarawa fattu kwanciya Adeeb yayi ajikinsa yana mai kallon fuskarta dake cike da tsoro,idanunta arufe gam, da hannunta shima ta rukunkume Adeeb dasu, idanunta kuma na tsiyayar da ruwan hawaye . Ahankali Adeeb ya sanya hannunsa yana mai share mata hawayen bakinsa ya kai daidai goshinta kamar zaiyi mata kiss saikuma yayi saurin dauke kansa . Ajiyar zuciya Adeeb yayi yana mai kallon sararin samaniya cike da jin wani irin shauƙi cikin zuciyarsa Manage please my people, Banda caji wllh nefa ya sami matsala. Mrs babi ce💘💘💘 Share and comment fisabilillah More comment More typing. [7/19, 7:01 PM] Abue Saleh AlQuyraemey: 🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄 MACIJI NE 🪱🪱🪱 Na mammy kabeer (Anty mammy Elegant online writers📚📚 Free book Page 27/28 https://www.facebook.com/groups/2803452939899949/?ref=share ________________Tafiya suke cikin sararin samani,yayin da Fattu ke ruƙunkume da Adeeb jikinta naci gaba da rawa,kuma har lokacin idanunta akulle suke. Ɗan juyowa Adeeb yayi yana mai kallonta ,shi mamakin tsoro irin na fattu yake,sam baiga abun tsoro ahawa jirgi ba,dubi yadda ta wani uzzurawa kanta,ko idanu ta kasa buɗe wa. Ni kuwa nace malam Adeeb fattu fa ko ganin jirgi baya taɓa yi ba ,bare ta hau,ai dole ta shiga cikin cakwakiya,akaranta na farko. Kallon fuskarta Adeeb keyi kamar bai taɓa ganin taba,haka kawai yake jin wani bakon al'amari tare dashi, jin yadda fattu ta ruƙunƙumeshin nan ,sai yake jin hakan yayi masa daɗi sosai,saidai yana tsoron abinda zuciya da gangar jikin sa ke ɓuƙatar aikatawa,idanu ya kirawo lips ɗinta ƙuri,cikin wani irin mugun son ya sunbacesu,gabansa sai bugawa yake,har wani lasar lips ɗin da yake ,yana hasko yadda zai sunbaci lips ɗin fattun.iyakar ƙokari Adeeb yayi dan hana kansa aikata abinda zuciyarsa ke tsananin muradi, amma ya kasa,dan jinsa yayi gaba ɗaya yanayinsa ya sauya ,ahankali cikin mugun son isar da saƙon zuciyarsa ya nufi ɗan bakin na fattu, har wani rawa bakinsa keyi, Yana gan da kai bakin nasa cikin nata ne ,fattu tayi waral!da idanunta,ma'ana ta buɗe idanun nata ba zato ba tsammani,karaf kuwa idanunsa ya sarƙe dana juna,da sauri Adeeb ya runtse idanunsa tare da kawar da kansa can gefe,saidai bai daga daga rankwafowar da yayi ba,jikinsa gaba daya yana manne dana fattun,wani irin abu yakeji mai kama da mayen karfe ,yana fusgarsa zuwa ga aiwatar da burinsa, kiss fa only kiss Adeeb you can do it ,dan ka samawa kanka mafita daga yanayin da kake ciki. Zuciyar Adeeb ke bashi wannan shawarar,ahankali ya ƙara bude idanunsa wanda suka fara sauya yanayi daga fari tas zuwa wani irin sirkin jaaa da wani ratsin pink. Kallon fattu yayi wacce itama shi take kallo tana wani rarraba idanu,Ita dai batasan me yake nufi ba,taga ya kwanto jikinta ne ,ƙila ahaka ake tafiyar ,amma kuma me yasami idanunsa haka,idan bata mantaba ,yanayin da idanunsa ya shiga yanzu,kusan kalar da idanunsa yake ne lokacin da yake macijinsa, kodai macijin zai ƙara zama ne?na shiga uku na idan yazama maciji yanzu yazanyi?ina zamuje cikin wannan halittar mai kama da kifi?nan da nan tsoro ya kama fattu ƙara rikoshi tayi sosai cikin muryar tsoro tace "Hamma menene?dan Allah karka ƙara zama maciji kai kadai nake dashi,idan ka koma maciji ya zanyi,waye zai fitar dani daga wannan cikin kifin da muka shi?ta faɗa cikin salon shagwaɓa taba mai zubda hawaye. Da ƙarfin gaske Adeeb ya runtse idanunsa, yana mai furta "ya Salam wannan yarinyar zata kashe ni fa"dan yanayin yadda tayi maganar ba ƙaramin tasiri yayi akan Adeeb ba,hakan saiya ƙara masa jin wani iri ajikinsa,gani yake kamar da gangan tayi hakan ma. Kansa banda juyawa ba abinda yake,yayinda zuciyarsa ke ta bashi shawarar kawai ya sunbaci fattun .cikin rashin sanin abinyi Adeeb ya ɗora bakinsa kan na fattu,ba tare da ɓata lokaciba ya fara kissing ɗinta kamar ya sami lolli pop,zaro idanu fattu tayi cike da tsantsar tsoro da mamaki,meye hakan kuma Hamma keyi?me yasa yake shan bakina?kodai shima yana cinye mutane ne?shikenan Ni fattu naga ta kaina ,wayyo Allah na,daga cikin fiki saikuma shanye baki?nan da nan fattu ta fara rawar jiki fiye da da,cikin zuciyarta tana take ta faman haure haure da ƙoƙarin ture Adeeb,amma kuma azahiri ta kasa koda ɗaga dan yatsanta ne bare tayi yunƙurin kwacewa. Shikuwa Adeeb ɗora bakinsa kan bakin fattu keda wuya ,gaba ɗaya haddarsa ta zube,tuni ya nemi inda kansa yake ya rasa,kissing ɗin bakin fattu kawai yake kamar Mayunwacin zaki. Kusan minti shida zuwa bakwai Adeeb na abu ɗaya,cikin kwancewar kai da rasa tunani,fattu kuwa tun tana jin abinda yakeyi kamar waiwayi yake mata har ta fara jin wani azababben zafi da raɗaɗi ,dan ji tayi kamar zai tsinke mata lips,tuni ta fara kuka tana ɗan bubbuga damtsen hannunsa. Hankali da tunanin Adeeb ne suka dawo jikinsa lokaci ɗaya,kuma ya fahimci abinda yake aikatawa da Fattun, cikin wata irin azama da hanzari ya dago kansa tare da cire bakinsa daga cikin na fattun. Da sauri ya zareta daga jikinsa yana mai mikewa cikin hanzari ya nufi wani daki,yana layi kamar ɗan maye. Yana shiga ɗakin ya kulle ƙofar tare da zamewa ajikin ƙofar ya zauna dabas. Dafe kansa yayi yana mai runtse idanunsa."meye hakan ?me na aikata kenan?wane irin kallo yarinyar zata rinƙa min yanzu?ohh my God ,why Adeeb !why am I losing my control over her?"Adeeb ya faɗa Afili yana mai tsakumo sukar kansa wacce ke kwance lub-lub. "Me ka aikata ba dai-dai ba Adeeb bakayi laifin komai ba ,kuma ba abin ƙi kayi ba just colm down"wani sashe na zuciyar Adeeb ne ke sanar dashi wannan maganar cikin yanayin rarrashi. Ahankali ya sauƙe wata ƙaƙkarfar ajiyar zuciya yana mai rarrafawa ya kwanta akan wani ƙayataccen gado dake cikin ɗakin.kwanciyar rigingine yayi tare da kumshe idanunsa.ba abinda ke masa gizo sai moment ɗin daya kasance cikinsa yanzu nan.tabbas bai taɓa jinsa cikin wata ni'imtacciyar rayuwa makaman iyar wadda ya fito daga cikinta ba yanzu,wannan yarinyar da yake mata kallon baby he can't imagine ace wai just kissing ɗin ta zai sanya shi cikin wannan yanayin ba. Kusan minti goma Adeeb ya ɗauka a kwance yana ta saƙa da warwara,gaba ɗaya ya kawowa kansa matsala,yana zaman zamansa ,yanzu inbanda amsawa ba abinda mararsa keyi. Tsaki yayi akaro na barkatai kafin ya mike cikin ƙarfin hali ya buɗe wata ƙofa ya shiga, wanka yayi ya tsarkake jikinsa kafin ya fito sanye da wata jallabiya, danaga ya buɗe wani guri ya zarota. Zama yayi abakin gadon daya kwanta dazu,yana tunani,me Yakamata yayi yanzu? Gara kawai ya fuske ya fita,idan ba haka ba yarinyar zata rinka masa wani iri. Kallo ne.dan haka mikewa yayi tare da ɗaure fuskarsa sosai kafin ya fito daga ɗakin. Fattu kuwa lokacin da Adeeb ya zareta daga jikinsa ,zama tayi atsorace kan kujerar jirgin tare da ƙanƙame jikinta,wani irin abu yakeji ajikin nata wanda bata san menene ba,gefe guda kuma lips ɗin ta dataji yana mata zugi,hannu ta kai tare da taɓa lips ɗin ta ,aikuwa jinsa tayi yayi tauri gurin,alamun ya kumbura kenan. Hannu ta sanya tare da share hawaye ta ,sannan ta kira kanta akan cinyarta tana kuka. Ita sam batasan meye hakan da Hamma yayi mata ke nufi ba,kuma gaba ɗaya jikinta yayi wani irin ,sam bata jin ƙarfi ajikinta,gashi har lokaci ji take kamar bakin Hamma nata yana cikin nata bakin.tana cikin wannan halin ne taji buɗe kofarsa . Firgigit tayi tare da zabura tana kallon inda taji ƙarar.haɗa ido sukayi da Hamma nata kallonsa take ƙuri ,ganin har kaya ma ya canja ,ko a ina ya sami kayan oho" Shikuwa Adeeb ganin sun haɗa idanu ya wani galla mata harara yana nufar kujerar dake dayan bangaren. Binsa da kallo fattu tayi tana mai son zuwa inda yake , amma tana tsoron yadda taga ya haɗe fuska. Ɗan juyowa Adeeb yayi jin cewar idanun fattu na kansa. Harara ya ƙara zabga mata cikin basarwa yace " karki cinyeni da ido fa,bayan kin gama cinyemin baki"ya faɗa yana saurin kawar da kansa,dan shi kansa saida yaji kunyar abinda ya faɗa.tunda yasan shine marar gaskiya . Fattu kuwa shiru tayi tana tunani,yaushe ta cinye masa bakin?kodai hankalin mutum yana gushewane idan yana cikin wannan abun,har yayi abu bai sani ba.dago kai tayi tana mai kallon Adeeb kafin cikin muryar mamaki tace "Hamma to meyasa na cinye maka bakin?kuma amma ai naga ga bakinka anan ajikinka, saidai ma ni nawa bakin dake min zafi " fattu ta faɗa cike da mamaki. Dariya ce taso kama Adeeb amma ya manne sannan ya kalleta yace" inaga kina da aljanu ko?haka kawai ki ka kama shamin baki kamar kin Sami sweet , shine zakice min bakinki na miki ciwo? "Na shiga ukuna Ni fattu Wllh Hamma bansan nayi ba ,nima kawai ganinki nayi kana shamin bakina kagani nan gurin ma ya kumbura ciwo yakemin"fattu ta faɗa tana ɗan turo kanta tare da nuna masa lips ɗinta na ƙasa wanda ya tasa. Kallon lips ɗin Adeeb yayi cike da jinjinawa wauta irinta fattu,sam bata da wayo ko kaɗan,kafin yace "maganinki ai garin don banzarki kika kuwa kanki ciwo ,Ni ba ruwana, kuma saikin faɗamin inda kika koyi wannan abunda kikayimin"Adeeb ya faɗa yana hararar fattu. Allah Sarki fattu kuwa tuni idanunta sun kawo ruwa,marairaicewa tayi tana mai juya kai,"Ayya Hamma nisa ba mayya ba ina zanyi wannan aikin mayyun,wllh bansan nayi maka ba dan Allah kayi haƙuri,nima bansan menene hakan yake nufi ba,amma idan kaji haushi ka rama kawai"fattu ta faɗa tana mai shashsheƙar kuka tare da goge wahaye,tsakani da Allah ita ina tasan ma tayi masa wannan abun,ita ba mayyaba ba komai ba ina ita ina shan bakin wani,ai ƙazantane ma wannan. Lallai ma yarinyar nan wato shine maye kenan ?hmmmm zakiyi bayanin maye.Adeeb ya faɗa cikin ransa yana mai jingina kansa da jikin kujera,dan sosai yaji kansa na ciwo wanan doguwar maganar da yayi. Bai ƙara cewa komai ba sai kumshe idanunsa da yayi ya jingina jikin kujerar,ba abinda yake gani sai lips ɗinsa cikin bakin fattu,ahankali yake sakin murmushi, ta gefen bakinsa,haƙiƙa al'amarin yayi masa daɗi sosai . Fattu kuwa ganin ya lunshe idanunsa yasa ta ɗan juya ta kalli window. Kan bala'i me zata fani,?gani tayi kamar ta saka hannunta ta kamo gajimare ,kuma saitaga kamar asama suke. Ɗan Dada leƙa kanta tayi sosai,yadda zata hango da gaske a sama suke ko a ƙasa,aikuwa wllh asaman suke,hana wani wawan ihu da fattu ta kurma tare da buga tsalle ta fito daga kan kujerar nan tayi kan Adeeb,ba Adeeb kadai ba ,hatta tareeƙ saida ya jiyo ihun fattu. Arazane Adeeb daya lula duniyar sa ta nishaɗi ya buɗe ido tare da mikewa tsaye cikin tsoro,kawai saijin fattu yayi ta fado kansa tana ihu"wayyo Allah na Ni fattu na shiga ukuna ,Hamma ka taimakeni,wllh duniyar sama suke tafiya ,dama saida nace bazan shiga cikin wannan kifin ba amma saboda mugunta ka shigo dani gashinan sai sama akeyi damu, wayyo Allah Hamma ka fitar dani daga nan wayyo baffa an,e....a.yyy.y..oooo ga....ji...immarr,sai kawai ta tafi luuuu tayi baya zata faɗi.alamun ta suma. Da sauri Adeeb ya dariya zuwa jikinsa,kumatunta yake ɗan bugawa yana faɗin"hey! hey!! wake up HULWA wake up please,Adeeb ya faɗa cikin mugun damuwa ,komawa yayi ya zauna tare da riƙe ta ahannunsa, dan bubbuga kumatunta yake yana kiran HULWA !HULWA,amma ina HULWA kam tayi kisan zango. Gefensa ya danna wata yar jar danja ,saiga wata ƙaramar ƙora ta buɗe ,ruwane da lemuka kala kala aciki da alamu dai fridge me,robar ruwan ya ɗauko tare da budewa,Ahankali yake tattara mata ruwan yana shafawa akan fuskarta amma ko motsi batayi ba. Hankalinsa yayi mugun tashi,sosai hannunsa ya kai saitin zuciyarta ya taɓa,da sauri kuma ya zare hannun nashi,sakamakon karo da yaci da tudun ƙirjin fattu. Ɗagota yayi tare da ɗora bakinsa kan nata ,sannan ya toshe hancinta,ya fara hura mata iska ,amma nan ma shiru,bayi motsiba, Cikin mugun tashin hankali Adeeb ya ƙanƙame fattu ajikinsa yana faɗin "AM sorry HULWA Please wake up " ya faɗa yana mai kara ƙankameta ajikinsa.nan da nan idanunsa suka fara rikiɗewa zuwa kaloli daban daban ,wani irin huci yake yana zazzage idanu jikinsa ya kama bari.idan kaga Adeeb a wanna lokacin tabbas zaka shiga cikin kuɗu da tsantsar tsoro ,dan gaba ɗaya kamaninsa sun sauya. Shiba mutum ba Shiba aljan ba. Cikin wanan halin suka sami isowa Misra,kai tsaye wani guest haose ɗin Adeeb na sirri Tareeƙ ya nufa ,suna sauka kuwa ,Adeeb ya kinkimo fattu da gudu yake sauka akan jirgin,kai tsaye yana zuwa jikin ƙofar ya fara daddanna wasu nonbobi jikin wata ƴar na'ura,cikin second kofar ta fara budewa tana faɗin well come back prince Adeeb Muhammad Ashraf , long time no see" kota kanta baibiba yayi cikin gidan da gudu,kai tsaye wani daki ya shiga ,yana zuwa bai jira wata wata ba daddanna wani guri tare da shigewa cikin wani ɗan banzan haɗaɗden jacuzy mai matuƙar girma da kyau,ruwane ya fara zubowa daga samansu, mai sanyi sosai,wanda idan haka kawai aka zubawa mutum ruwan nan tabbas sai yayi jinya. Bubbuga kumatun fattu yaci gaba dayi yana kiran sunanta"HULWA ! HULWA!! HULWA!!! Har sau uku,Ahankali fattu ta fara bude idanunta tana lumshewa, kafin ta buɗe su duka, da sauri kuma ta ƙankame Adeeb tana mai cewa"dan Allah Hamma kafitar dani dana cikin kifin na wllh tsoro nakeji,Hamma, fattu ta faɗa tana mai rawar jiki. Janyota Adeeb yayi zuwa jikinsa yana mai sakin wata kakkarfar ajiyar zuciya,"AM sorry HULWA ba abinda zai sameki ina tare da ke ,Please karki ƙara suma irin haka,saura kaɗan zuciyata ta buga" ya faɗa cikin rashin sanin abinda yake faɗi. " Hamma mufita dan Allah" fattu ta sake faɗa. Ahankali Adeeb ya riƙe kumatun fattu yana kallonta kafin yace "ki nutsu HULWA ba acikin jirgin muke ba yanzu,mun fita kalli kigani we are in toilet now ,bazan taɓa barin wani abu ya samekiba ,domin kuɗin mallakina ce kuma amanata, sannan ma....saikuma yayi shiru ,tare da cire hannunsa daga kan fuskar ta,fitowa yayi daga cikin ruwan ,sannan ya kamo hannunta ya fito da ita ,sai rawar sanyi yake,wani ɗaki ya kaita tare da zaunar da ita akan wani makeken gado,a baidamu da yadda jikinta ke jiƙe ba,wani ƙaton bargo ya dauko ya lulluɓa mata,sannan ya nufi jikin wani bango,nidai naga ya danna wani guri,kawai naga bango Ya dare,kaya sun bayyana.ehe mana bango Ya dare zance,tunda idan ka kalli gurin bazaka taba tsammanin akwai wata ƙofa dazata bude ajikinsa ba. Wasu kaya naga ya dauko masu kama dana sanyi riga da wando sannan. Ya dawo kusa da fattu da ke binsa da kallo yace "kisa wannan kayan ,kinji,zanje in shirya nima yanzu zan dawo " ya faɗa yana mika mata kayan. Karba tayi cikin rawar hannu tana mai binsa da kallo harya fice daga ɗakin. Bin dakin fattu tayi da kallo,ikon Allah wai nan ɗin ɗakin mutum ne ,saikace wanda aka tattaro duk kayan jin daɗin duniya aka ajiye aciki. Ahankali ta mike ta cire kayan jikinta sannan ta sanya riga da wando da Adeeb ya bata,kayan sunyi mata kyau sosai,saidai wando yayi mata tsayi rigar ma haka,kasancewar Adeeb dogone sosai,hakan yasa rigar ta sauƙo ta rufe mata manyan mazaunanta.sanna kuma rigar tana da hula,hmmmmm nan da nan fattu ta koma wata irin ƴar balarabiyar nan tayi mugun kyau cikin kayan . Kayan data cire ɗin ta dauka tare da rikews ahannunta tana tsaye ,tana waige waige kallo ɗaya zaka mata kasan afirgice take. Bude ɗakin Adeeb yayi bayan yayi noking yaji shiru, "Masha Allah " shine abinda Adeeb ya iya faɗi lokacin da yayi arba da fattu cikin kayan nan. Shima yana sanye da wata farar jallabiya ajikinsa da hirami akansa.yayi kyau sosai cikin shigar tasu ta larabawa. Cikin ɗakin ya nufa yana mai jure fattu da idanu,ita kuwa kanta na ƙasa,riƙe da jiƙaƙkun kayanta. Cikin wata irin murya mai kama da mutum na jin barci Adeeb yace "Hulwa" Ahankali fattu ta daga kanta tana kallon bayan Adeeb ɗin dan gani ta ina hulwar zata fito..... DOMIN SAMUN LITTAFIN COMPLETE SAI KU TAƁA BULUN RUBUTUN DAKE KASA 👇🏻👇🏻👇🏻 https://www.aihausanovels.com.ng/2022/07/macijine-shi-page-21-22-hausa-novel.html Muje zuwa masu karatu, Mrs babi ce💘💘💘 [7/21, 11:20 AM] Abue Saleh AlQuyraemey: 🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄 MACIJI NE🪱🪱🪱 Na mammy kabeer (Anty mammy) Elegant online writers📚📚 Free book Page 29/30 _________________Cikin wani irin salo da murya mai maka da yana jin barci,Adeeb yace "Hulwa" Ahankali fattu ta dago kanta tana mai kallon bayan Adeeb ɗan ganin ta ina hulwar zata fito. Rarraba idanu take ,amma bataga kowa ba,ikon Allah ko ina hulwar take ?bisani Banga kowa abayansa ba ,kuma ba kowa cikin ɗakin nan, fattu ta faɗa tana mai waige bayanta ,dan ita dai bataga hulwa anan ba. Duk abinda take Adeeb na kallonta,kuma ya gane me take nufi,wato suna daya faɗa shine bata ganeba,take neman mai sunan. Juyowa fattu tayi ta kalli Adeeb ɗin cikin rashin fahimta tace "Hamma Ina hulwar take ?naga ba kowa cikin ɗakin nan ? Kallonta yayi tare da ɗan zafi ido yace "yanzu ke bakuga hulwar tawa ba anan?" Ya faɗa yana mata kallon tuhuma. Waigawa fattu ta sakeyi bayanta,amma wllh ita kam bataga kowa ba,juyowa tayi tace "alƙur'ani banga kowa ba" ta faɗa tana ɗan buɗe hannayenta dan tabbatar masa da cewar ba kowa aɗakin. Yaɓe baki yayi yace "matata ce hulwa kuma gata nan akusa dani idan ke bakya ganinta toni ina ganin abata,ya faɗa yana ɗan kallon kusa da gadon da fattu ke tsaye. Ai fattu najin haka wani irin tsoro ya kamata,da gudu ta watsar da kayan hannunta ta taho gareshi ,tana zuwa ta biye abayansa tana tsuma, ahankali take masa faɗa cikin kunnensa,"aradu Hamma aljanna kake gani ba matar ka ba,dan ba kowa acikin ɗakin nan,Ni dama tun dazu nakewa dakin kallon na aljanu,dan wannan ɗakin baiyi kama dana mutane ba ,kyanshi yayi yawa aradun Allah" fattu ta ƙare magannarta cikin kunne Adeeb da sunan tana masa raɗa dan kar Hulwa tajisu. Tunda ta fara masa magana akunne ya wani lumshe idanunsa,har cikin ƙwaƙwalwar sa yake jin sautin maganarta, yayi da yake jin tana zaga dukkan ilahirin jikinsa, wani yuuuuum yakeji ajikinsa har kamar zai faɗi.ahankali ya buɗe idanunsa,jin ta kai aya akan maganar tata. Wacce shidai yaji farkon,amma sam bai fahimci me take fadi ba daga ƙarshen. Yana shirin yin magana ne yajiyo ƙarar na'urar sanarda mutum yayi bako tana faɗin tareek na jikansa afalo. Dan haka ya fasa yin maganar ,kawai saiya juyo yana kallon fattun da tunanin idanunsa,ahankali ya buɗe baki da gyara yace "wait for me here I will be back" ya faɗa yana ƙoƙarin buɗe kofar,ai carab fattu ta kama hannunsa ta riƙe cikin nata gam!tana kallonsa. Kallonta yayi shima da nuna alamun menene? Turo baki tayi tace " Ni ma zan bila Hamma,dan naji ka kira sunan wasu mutanen da yawa,bayan waccan hulwar Ni wllh tsoro nake ji" fattu ta faɗa tana mai kallon fuskarsa. Hannunsa data rike cikin nashi,yabi da kallon,kafin ya ɗago yana kallonta,waima shi yaushe ya kira sunan wasu mutane kuma?ahankali ya sanya hannu ya zare nata hannun daga nashi kafin yace"bazaki bini ba, kuma Ni nace ne ki Kijirani kawai"ya faɗa yana harararta tare da bude ƙofar,yana sanya ƙafarsa waje fattu ma ta fito jikinta sai rawa yake,juyowa yayi yana kallonta fuska ba walwala yace " koma" Marairaicewa fattu tayi kafin tace " wllh tsoro nakeji,dan Allah kaje dani,wannan hulwar fa tana ciki" harara ya Banka mata kafin yace "get in I said ,hulwar ta cinyeki" ya faɗa yana turata ciki dakin yana ƙofar ya kulle. Hauka yake yaje da ita gurin tareek cikin wannan shigar?ai wllh idan tareek ya ganta ahana,inaga saina kusan mutuwa dan baƙin ciki.cewar Adeeb kenan yana nufar madaidaicin falon daya gaji da hadewa,zama yayi yana kallon tareek ɗin cikin yanayinsa ya haɗe fuska. "Yallaɓai me yake faruwa ne ?naga ka shigo cikin tashin hankali?"tareek ya faɗa cikin harshen larabci yana kallon Adeeb ɗin. Ajiyar zuciya Adeeb yayi kafin ya jingina kansa jikin kujera ,kusan minti biyu kafin ya buɗe baki dagyar yace " ta tsoratane ,shine ta suma" shima cikin harshen larabci yayi maganar. "Ya Salam, yallaɓai koka sanar da ita wanann maganar ne?" "No ban faɗa mata ba" cewar Adeeb . Shiru suka ɗanyi na wani lokaci, kafin tareek yace "yallaɓai abie baisan da dawowarsa,bansanar da kowa ba kamar yadda ka buƙata" Ɗagowa Adeeb yayi daga kwanciyar da yayi jikin kujera,kafin yace " Yes,bana son ya sani yanzu,sai dare yayi zamuje gurinsa, ka shirya komai da komai,yanzu zanje na rage suman nan ne" Adeeb ya faɗa yana mai shafa dogon lallausan gashin kansa zuwa gefen fuskarsa da gemunsa. "Ok me kake ɓukata yanzu yallaɓai " tareek ya faɗa cikin ladabi. "Kaje ka kawo mata kayan buƙata duka, sannan ka tahomin da wayoyi ayi duk abinda ya kamata" yana faɗin haka bai jira me Tareek zaiceba ya miƙe tare da nufar wani ɗakin da ban. Fattu kuwa Adeeb yana kulle ƙofar taji wani mugun tsoro da fargaba, wayyo Allah,yanzu ya zanyi idan hulwar nan mai shan jini ce ? Kuma gashi bana ganinta ? Zama tayi agurin tare da ƙanƙame jikinta tana kuka sosai harda shashsheka,Allah Sarki baffanta ,ko wane hali yake ciki yanzu?ko wane hukunci mai gari ya ɗauka akansa? Allah dai ya kare mata baffanta Aduk yanayin daya tsinci kansa. Tana nan zaune sai waige waige take ,ta gaji sosai ga yunwa ,ga barci,gashi tana sonyin salla dan rabonta da abinci tun wanann jakwalkwalon da Hamma ya bata awanann gidan.tana zaune shiru kawai taga wasu labulaye masu suna saukowa ahankali daga kowane bango na ɗakin.wata zabura da tayi cikin tsoro ta kwallah ihu tana mai komawa tsakiyar dakin ,banda rawa ba abinda jikinta keyi"wayyo Allah ma hulwa dan Allah kiyi haƙuri,karki cinyeni ,wllh ba abinda nayi miki,Hamma ne ya kawoni gidanki"abinda fattu ke fadi kenan tana rawar jiki da karkarwa,tana juye juye atsakiyar dakin,ta kalli wannan bangon ta kalli wancan.. Sukuwa labulaye ,sai sauka suke kasa,kuma basu tsayaba ,saida suka dire har aƙasa. Sai kuma taga hasken ɗakin ya sauya kala ,daga farin haske zuwa dim light,kuma daga can gefe wata bishi sai walwali take . Kuka sosai fattu keyi cikin tsoro da rashin sanin abinyi,yaukan yasan kwananta kawai ya kare kamar wacce akace kalli can ,tana juyowa wajen da sif ɗin nan take ,kawai taga abubuwa kamar malam bude mana littafi, suna ta yawonsu ajikin sif ɗin. Wata irin numfashi fattu ta jaa da ƙarfi,kafin kuma tayi ƙasa sululu ta faɗa kan gadon asume. Shikuwa Adeeb yana shiga wannan dakin kwanciya ya ɗanyi akan lafiyayyen gadon dake ɗakin,so yake ya ɗan huta,dan gaba ɗaya yarinyar nan ta gama gajiyar dashi ,yana kwanciya sai yayi tunanin ai baiyi Sallah ba,dan haka tashi yayi tare da sake wanka sannan yayi Sallah,ya koma toilet ɗin ya gabata fuskarsa,sosai naga kyansa ya ƙara fitowa ,ashema kyanshi ya wuce yadda nake tunani,dan kallo daya idan kayi masa ,kuma kuka haɗa idanu ,bazaka iya ƙara yarda ku haɗa ido ba,dan yana da wani irin kwarjini da haiba. Wannan karon ƙananan kaya ya sanya,riga da wando ne na jins, rigar light blue ce ,yayinda wando kuma ya kasance blue ne sosai.kansa ya taje, sannan ya fashe jikinsa da tauraruwa masu masifar ƙamshi, danaga ya buɗe wata loka guda ,duka turarukane acikin lokar tunda ga sama har ƙasanta. Wata lokar ya buɗe naga agoguna ,masu azabar kyau da tsada,wani agogon kwal ya dauko ya daura ahanannunsa, sannan ,sannan ya buɗe bangaren takalma,nidai gefe na koma na zama yar kallo.dan abun yafi karfina, daki guda duka na kayan Amfanin mutum ɗaya?wani aikin sai amasar. Yana gama shiryawa ,dakin ya dauki wani ƙamshi mai rikitarwa da sanya nutsuwa,kanshi ya taje sannan ya shafa mayuka kusan kala biyar akan nashi,tuni kan ya dauki walwali da sheƙi, Fitowa yayi daga ɗakin ya nufi kitchen,masu karatu kuzo kuga kitchen ,aini kodaga nam aka barni ,tabbas na more,dan iya tsaruwa kitchen ɗin nan ya tsaru. Wani irin tea naga ya haɗa ,sannan ya siya kwai tare da imdomie,shikam arayuwarsa baida wani abinci daga tea sai imdomie saiko nama, Yana gama haɗawa ya tsaya yana kallon abincin daya haɗa ɗin cikin wani kayataccen faranti, mamakin kansa yake ,wai yau shine da haɗawa wata abinci,kuma shi zai kai mata da kansa.koda yake ai itaɗin amanar sa ce,kuma dole ya kula da ita. Ɗaukar tiren yayi ya nufi dakin da Fattun ke ciki, Kwankwasawa yayi kafin ya dannan wani guri sai ga kofar tana komawa gefe guda,harya buɗe gaba ɗaya ɗaya . Kansa ya kunna cikin dakin yana mai kallon yadda komai ya canza,wannan alamun e na lokacin barcinsa yayi ,dama haka dakunan aka shiryasu suke sauya komai da kansu,idan lokacin barcin rana ne kona dare ,kokuma safiya . Ajiye tiren yayi yana mai kallon ta ina zai hangi fattu,can ya hangota kwance akan gado ,saidai da'alama kwanciyar bata daɗi bace, dan haka da sauri ya nufeta, kamar yadda yayi tsammani kuwa suma tayi,cike da fargaba ya ɗagota yana mai kiran sunanta ,"Hulwa !hulwa!!amma bata ko motsaba,ajiye ta yayi tare da bude fridge ya dauko ruwa mai sanyi yana yayyafa mata.amma bata ko motsaba ,wai wannan suman na menene haka?duka duka yaushema ta dawo hayyacinta ne ?gashi yanzu ta ƙara suka. Huci kawai yake yana kallon fuskarta,zuciyarsa kamar zata fasa ƙirjinsa ta fito,sam baya ƙaunar ganin fattu cikin wani mugun yanayi,waima menene yayi silar wannan suman nata ne?kallon dakin yayi yana mai jinjina kai ,ba shakka tayi arba da yadda dakin nan ke sauyawa ne,wani irin runtse idanunsa yayi tare da dafe kansa,duk laifinane dana fita da ita da duk haka bata faru ba.bude idanunsa yayi wanda suka juye zuwa na macizai sak, ahankali jikinsa ya kama wata irin girgiza yana hayaƙi,kan kace me saiga ɗakin ya turnuƙe da hayaƙi, kusan minti biyar dakin yana wanann yanayi hayaƙi da wata irin ƙara,kafin hayaƙi ya baje, saiga wani murtukeken maciji mai girman gaske ya fasa kai yana huci. Cikin tafiyar macizai macijin nan ya fara sauƙa daga kan gadon ,bangon dakin ya kama tare da fara lauye jikin wanan haɗaɗdun labulayen yana nannadesu tare da fesa musu wani irin ruwa daga bakinsa,da zaran ya fesa ruwan sai kaga labulen yana hayaƙi tare da murmushewa, haka yayi tayi saida ya bata gaba dayan labulayenan sannan ya fara bugun kwayayen dakin dake bada hasken nan mai ban sha'awa da jelarsa.tas saida ya gama fashesu, sannan ya nufi kan gadon,yana zuwa ya hau kan cikin fattu dake kwance ,cikin halin suma,zagayeta ya farayi tare da shigewa ciki rigarta sosai,yana goga mata sanyin dake jikinsa. Aikuwa sanyin yana fara ratsa fattu ,ta fara bude idanunta ahankali,tana mai dafe kanta tare da yamutse fuska. Abu taji yana fitowa sululu daga cikin rigarta,da sauri ta tashi zaune tana mai daga rigarta sama,daidai lokacin shikuwa macijin ya gama fitowa daga jikin nata. Saƙare fattu tayi tana kallon macijin cike da tsantsar mamaki,shima macijin kallonta yake ido cikin ido. Masu karatu meke faruwa ne? Wannan macijin kuma waye? Shin Adeeb dama bai daina zama macijin ba? Muje zuwa takuce anty mammy Domin Sauke Cikakken Littafin Sai Ku Danna Bulun Rubutun Dake Kasa 👇🏻👇🏻 https://www.aihausanovels.com.ng/2022/07/macijine-shi-complete-novel.html Mrs babi💘💘💘 Share and comment Fisabilillah. More comments More typing. [7/22, 6:06 AM] Aishat Anty: 🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄 MACIJI NE🪱🪱🪱 Na mammy kabeer (Anty mammy) Elegant online writers📚📚 https://facebook.com/groups/943534712916776/ Masu amfani da Facebook sai kuyi join wan nan link din👆🏽 Free book Page 31/32 _________________Saƙare,fattu tayi tana kallon macijin cike da tsantsar mamaki, kamar yadda macijin ke kallon fattu shima ido cikin ido. Ahankali fattu ta lumshe idonta,tana mai ambaton sunan Allah,abin da ya bata mamaki shine,sam bataji tsoroba, saima bin jikin macijin da tayi da kallo,tabbas wannan macijin ta ne na yar ruga, kenan hakan na nufin Hammanta ne ya ƙara zama maciji? innalillahi ,yanzu yazatayi kenan?awane matsayin take idan bai dawo mutum ba? Ahankali ta furta "Hammana" hawaye na zubowa daga cikin idanunta. Shikuwa macijin yana ganin hawayen nan nata,ya taho zuwa gareta,yana zuwa ya hau kan cinyarta tare da nannaɗe jikinsa ya ɗora kansa akan kafaɗunta. Lumshe ido fattu tayi cikin kuka tace " dan Allah HAMMA karka zauna cikin wannan yanayin,bazan iya rayuwa Ni kadai cikin wannan gidan mai aljanu ba, dazuma saida Hulwarka tazo ta tsoratani, gaba daya ta sanja duniyar wannan dakin ,ya koma wata kala,kalli kagani yanzu yadda ya koma,Hamma inajin tsoro"fattu ta faɗa tare da ɗora hannunta akan macijin tana shafawa. Dagowa macijin yayi tare da zuba mata idanu,itama kallonsa take hawaye na zubowa daga idanunta. Jikinta ya fara zagayewa yana yana nannaɗeta,kafin kuma yayi baya da ita akan gadon,kwanciya fattu tayi tare da runtse idanunta . Ita kam tariga ta gama sallama wa rayuwa, tasan idan har macijinta bai dawo mutum ba to mutuwa zatayi, ahalin da ake ciki yanzu tana jinsa ne har cikin ranta,kome takeyi shi take gani,ba abinda take bukata akullum kamar tajita kusa dashi,ta san duk ransa wani ya ganshi matsayin maciji ,to za'ayi ƙoƙarin kashe mata shine,wanda tayi imanin duk randa aka kashe Hamma, to tabbas da gawarsa za'a binnesu. Shikuwa maciji bayan ya kwantar da fattu saiya zare jikinsa daga nannaɗetan da yayi,sannan ya kamo bargon dake kan gadon ya lullaba ajikin fattu,duk abinda yake kallonsa fattu keyi cike da tausayawa,ace mutum yana komawa wata da bar daban?kuma mai haɗari wacce kowa ke gudunta.saukowa yayi daga kan gadon tare da tsayawa daga can gefenta yana kallonta, itama kallonsa take ,kusan minti uku suna kallon juna,yayin da fattu ke zubda hawaye,juyawa yayi tare da nufar ƙofar dakin. "Dan Allah Hamma ka dawo mutum,kada ka tafi ka barni,ina don kasancewa tare da kai,bani da kowa awannan sabuwar duniyar saikai"abinda fattu ta faɗa kenan lokacin da taga yana ƙoƙarin ficewa daga ɗakin. Aikuwa tsayawa yayi kamar wanda yake sauraron me take faɗi .saida ta kai aya azancenta,kafin ya kalleta da idanunsa masu naunuka daban daban,sannan ya fice daga ɗakin. Kuka sosai fattu ta fashe dashi,tana daga kwancen nan,shikenan komai yazo mata ƙarshe,idan Hamma ya tafi ya barta,ita ahalin yanzu ma, ta fara tunanin kodai duniyar aljanu ya kawo ta? Haka tayi ta kukanta tana daga kwance har barcine wahala yayi gaba da ita. Shikuwa Adeeb yana fita kai tsaye dakin daya baro ya nufa ,ahankali yake jan jikinsa , harya kai kan gadon ,hawa yayi tare da kwantawa lamo kamar baya nunfashi,rufe idanunsa yayi yana nishi da gyar, kafin kuma jikinsa ya kama girgiza sosai yana hayaƙi, sosai dakin ya turnuƙe da hayaƙi kafin ya washe. Ikon Allah Adeeb na hanga kwance akan gadon nan,ya duƙunƙune jikinsa,sai rawa yake kamar mai jin sanyi,ahankali ya ɗaya hannunsa dake ta faman rawa ya dage kansa,yana mai yamutse fuska ,da alama kan ke masa ciwo,kusan minti goma ya ɗauka cikin wanan halin kafin naga ya miƙe jiki ba kwari,ya nufi toilet ,wanka yayi tare da sake kaya,ya fito cikin fara tass ɗin jallabiyya. Zama yayi akan wata kujera dake gaban gadon,kujerar tsabar kyanta ,kai kace da zallar kwal akayita.sai ƙamshi yake bugawa, kallon ɗakin yake yana mai mamakin shidai yasan ya fita zuwa kitchen kuma har yayi girki,bayan nan kuma ya nufi dakin Hulwa, kuma... Da sauri ya mike yana mai zafi ido,tabbas asume ya ganta aɗakin ,amma kuma me yasa shi yaganshi ana ?me ya dawo dashi ɗakinsa. Da sauri ya nufi ƙofa yana ficewa daga dakin,saidai yana fita kafin ya kai dakin nata,yaji sanarwar zuwan tareeƙ,kallon kofar Tata yayi sannan ya nufi bakin ƙofar shigowa falon, yana ɓudewa ya ga tareeƙ da kaya riƙi-riƙi ahannunsa. Kallonsa tareeƙ yayi yace "yallaɓai lafiya kuwa? Ahankali Adeeb ya lumshe idanunsa kafin ya jinjinawa tareek din kai,alamu lafiya ba komai. Shigowa tareeƙ yayi da kayan ya ajiye yana mai cewa"yallaɓai idan an duba sai afadamin abinda babu aciki." Nan ma dai kai kawai Adeeb ya daga sannan ya kalli kayan ,ledojine kusan guda goma manya-manya. Kallon Tareeƙ yayi na dan wani lokaci kafin yace "an shirya komai na zuwan gurin mai Abie"? " Eh yallaɓai komai ya kammala ,lokaci kawai muke jira" cewar tareeƙ kenan cikin girmamawa . Jinjina kai Adeeb yayi kafin yace " U can go" "Ok yallabai" Tareeƙ ya faɗa yana mai barin falon . Kayan da tareeƙ ya ajiye Adeeb yayi da kallo kafin ya ɗauki leda ɗaya yana ɗan leƙawa, idanunsa ne suka sauka kan inner wear masu bala'in kyau da tsada,da sauri ya rufe ledar yana ɗan kallon ƙofa, dan sosa kansa yayi kafin ya dauko bra guda ɗaya da hannunsa yana mai kallonta,shiru yayi yana tunanin lallai zatayiwa fattu daidai,dan ahalin yanzu yana kallon abubuwan ta daya taɓa gani a toilet,murmushin yay tare da dan sosa kansa kafin ya ɗauki ledojin duka ahannunsa yayi dakin fattun. Yana tura ƙofar kuwa ya jiyo ƙinkishin kukanta,tana zaune a tsakiyar gadon ta haɗa kai da gwuiwa tana kuka.dan bata wani jima tana barcin ba ta farka kuma ita tsoro takeji taje ta taɓa kofar wannan hulwar ta kuma tsoratata. Da sauri ya ƙarasa cikin dakin yana kallonta,tsayawa yayi akanta bayan ya ajiye ledojin dake hannunsa,sosai yake jin tausayin fattu cikin zuciyarsa,sam baya kyaunar ganinta cikin damuwa,yanzu zaiji zuciyarsa tayi masa zafi sosai. "Hulwa " Adeeb ya furta cikin muryarsa mai sanyi da nutsuwa. Da sauri fattu ta ɗago kanta ,sakamakon jin Muryar Adeeb da tayi, Ai bata san lokacin data diro daga kan gadon nan ba ta wani ƙanƙame Adeeb da iya ƙarfinta tana kuka, "Hammana dama nasan bazaka gudu ka barni ba, Hamma na shiga damuwa sosai lokacin danaga ka koma macijin nan,nayi tunanin guduwa zakayi ka barni Hammana dan Allah karka rabu dani"fattu ta faɗa cikin matsanancin kuka,wanda zamu iya cewa na farin cikine. ahankali Adeeb ya lumshe idanunsa,tare da sakin ajiyar zuciya"har abada bazan taba rabuwa dake ba,ina tare dake komai rintsi komai wuya hulwatee" abinda Adeeb ya faɗa kenan , cikin zuciyarsa,amma azahiri kawai rungume fattu yayi shima ,yana mai shafa bayanta ahankali. Kuka sosai fattu keyi tana kara rungume Adeeb,bazata iya faɗin irin farin cikin da take cikiba, " Ya isa haka kukan " Adeeb ya faɗa yana mai ɗago kanta.komar da kan nata tayi tare da kara kwanciya akan faffaɗan ƙirjinsa. Murmushi kawai Adeeb ya tsinci kansa dayi,yana mai shafa bayan fattu,sosai yake jin wani nishadi idan fattu ta ruƙunkume shi nan ,ji yake kamar su tabbata ahaka. Bangaren Fattuna dai hakan ne ,ji tayi bata don rabuwa da jikin Adeeb ɗin,dan ba ƙaramin nutsuwa take samu akan wannan ƙirjin nashiba. Kusan minti goma suna rungume da juna ,kafin Adeeb yayi karfin halin cire ta daga jikinsa yana mai cewa" waike bazai sakeni ba saikin karyani?kin fiye son jiki fa" ya faɗa yana ɗan harararta . Kai ta duniyar ƙasa kafin tace "Hamma yunwa nakeji" kallon inda ya ajiye abincin dazu yayi kafin ya janyo table ɗin zuwa gaban gadon, " Zauna "yace mata. Zama tayi abakin gadon tana kallonsa,farin ciki fal cikin ranta. Tea ya haɗa mata sannan ya mika mata flate ɗin kwan da bread zuwa gabanta.wani bowl ya mika mata ta wanke hannunta,kafin ta fara cin abincin,lallai fattu na jin yunwa ,dan kuwa tass ta kawar da abincin nan,shidai kallonta kawai yake,azuciyarsa yace "wannan badai ciba" tana gamawa tayi hamdala tana mai lashe lips ɗinta,ɗago kai tayi suka haɗa ido da Adeeb ,saikuma kunya ta kamata,ganin yadda ta kawar da uban abincin nan. Shikuwa Adeeb cewa yayi " kin koshi ko zaki ƙara dan naga kedin akwai ci kamar Gara" Dan shagwabe fuska tayi kafin tace "Allah Hamma abincinne ke wuce silik -silik,ba dan ma na cinyeba.ta faɗa tana kallon farantin. Ƙureta kawai yayi da ido yana kallonta baice komaiba,dagowa tayi suka haɗa ido ,harararta yayi yace "zaki fara kallonsa ko" girgiza kai tayi tare da maida kanta ƙasa."zanyi sallah Hamma"ta faɗa kanta a ƙasa. Nuna mata toilet yayi da hannunsa ,ba tare da yace komai ba. Mikewa tayi yake bakin ƙofar ta tsaya tare da juyowa. Yana kallonta baice komai ba,dan yasan me take nufi,ita komai bata iyaba Saida yayi jimmm!kafin ya mike ya ƙarasa jinkin ƙofar, ya murda handle ɗin yace "kin gani haka ake yi"jinjina kai tayi tare da mamakin wai ƙifama sai anwani murɗata kamar kan fanfo" Maida ƙurar yayi ya kulle sanan yace "buɗe"kallonsa tayi kafin ta kalli ƙofar, hannunta ta sanya tayi kamar yadda yayi aikuwa saiga ƙofa ta bude.wata dariya ce ta kwacewa fattu ganin tayi nasarar buɗe kofar tace " hahhahhh laaaah Hamma dan Allah kaga abin sauƙi wllh kuma budewa daɗi"ta faɗa tana kara sanya dariya cikin farin ciki. Shikansa Adeeb dariyar tayi har saida fararen haƙoransa suka bayyana.jijjiga kai yayi kafin ya wuce ciki yana faɗin"Allah ya shiryeki" Komai saida ya nuna mata ,sanan yasa ta kunna da kanta,aikuwa fattu gaba ɗaya yau ta zama kamar wata shasha ,data kunna abu yayi zata kama dariya,wataran harda ɗan tsallenta takeyi. Shidai fitowa yayi ya barta dan tayi wanka da alwala. Bude kayan da tareeƙ ya kawo yayi ,wata doguwar pink ɗin riga ya dauko da mahaifinta ya ajiye mata,sannan ya dauko wani fant da bra ya ajiye akan gadon,sannan fice. Bayan fattu tayi sallah ne taga kaya akan gado,ɗauka tayi tana kallon kayan,sunyi mata kyau a ido sosai ,amma saita ajiye da sauri tace "ƙilama na hulwar tasane ,Ni wllh na tsani wannan hulwar" ta faɗa tana hararar kayan. Adeeb me ya shigo cikin dakin da sallama can ƙasan maƙoshinsa. Tsayawa yayi yana kallon fattu ganin bata sake kayan daya ajiye mata ba. " Baki Ga kaya bane kika maida wannan. Dan ƙazanta" Adeeb ya faɗa tana hararar fattu. "Kayi hakuri Hamma nayi tunanin a hulwar taka ne ai" fattu ta faɗa tana daga kayan, "Hamma wannan fa " ta faɗa tana daga bra ɗin nan. " Baki san me ake yi da itaba maza ki shirya ina jiranki" ya faɗa harararta tare da ficewa daga ɗakin. Fattu kuwa data rasa ya zatayi da bra ɗin na sai kawai ta sanya kayanta haka tayi waje . Tana fitowa Adeeb ya biya da kallo ganin bata sanya bra dinba ,yace ........ Mu hade next page banda cajine. Mrs babi ce💘💘💘 [7/22, 10:09 PM] Aishat Anty: 🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄 MACIJI NE🪱🪱🪱 Na mammy kabeer (Anty mammy) Elegant online writers📚📚 Free book Page 33/34 ________________Fattu kuwa data rasa inda zata maƙala wannan abun ,sai kawai ta sanya kayanta haka ta yi waje gurin Adeeb, kafin ta fita daga ƙofar saida ta buɗe ta rufe kusan sau biyar,idan buɗe saitayi dariya ta ƙara rifewa, sannan ta buɗe,murna take sosai itama yanzu ta iya buɗe kofar yan wata duniyat. Tana fitowa kuwa Adeeb ya bita da kallo, so yake yaga ko tasaka wannan abun,saidai kamar yadda ya tsammata ,bata saka ɗin ba kuwa,dan haka kallonta yayi tare da dalla mata harara yace " kingama shiryawa kenan?" Kai fattu ta daga masa tana gyara lullubin da tayiwa matakin kamar wata amarya,ta rufe kusan rabin fuskarta ,sannan ta kama wuyan ta rike ƙam da hannunta. Shiru yayi yana ɗan wani tunani,shi baisan ta yaya zai faɗa mata cewar tasaka bra ɗin ba,dan haka sai yace" ina wannan abun da kika tambayeni na menene?"ya faɗa yana kallonta. Itama kallonsa tayi kafin tace " na barshi agurin ne ,dan bansan a ina ake sakawa ba" ta faɗa tana ƙara riƙe wuyanta, dan kar mayafin ya faɗi. Kallonta yayi har zaiyo magana sai kuma ya fasa ,wayoyin da tareeƙ ya taho masa da su ya ɗauki daya daga ciki , ya daga tare da kiran tareeƙ . Yana dagawa yace "ka tahomin da make up artist yanzu ta shirya yarinyar nan" "Ok sir " tareeƙ ya faɗa yana mai kiran wata number. "Koma daki" Adeeb ya faɗa yana mai mikewa shima ya bar gurin.juyawa tayi ta koma tana mai tunanin kodai tayi masa wani abunne ? Taji yace ta koma ɗauki?zama tayi bakin gado tana mai cire mayafin nan ,dama duk ya isheta.gashin kanta ta shafa,tun wannan daurin dake kanta ,shine har yanzu,kuma kan nata ƙaiƙayi yake mata amma Indai ta zata ƙaramin wanka saita nemi omo ta wanke kan dashi . Ba komawa saiga tarin ya shigo gidan,waya ya kira Adeeb yake sanar dashi sun karaso. Cewa Adeeb yayi ya nuna mata ɗakin farko shikuma yashigo ɗakin hutu. Kasancewar ba inda tareeƙ bai sani ba acikin gidan,dan haka ya nunawa matar wacce take balarabiya ce dakin yace tayiwa yarinyar ciki duk abinda ya dace . Shikuma ya shiga dakin da Adeeb ke ciki. Da sallama ya shiga dakin,Adeeb na kwance akan gado, ba barci yake ba ,amma idanunsa alumshe suke .zama tareeƙ yayi yana mai cewa" yallaɓai fatan dai kana cikin ƙoshin lafiya" Ahankali Adeeb ya yunƙura ya tashi zaune,kallon tareeƙ yayi kafin ya sauke ajiyar zuciya yace " tareeƙ ina tunanin abinda nayi ne ,kada yarinyar nan taga kamar na cutar da itane"Adeeb ya faɗa yana kallon tareeƙ da yanayin damuwa akan fuskarsa. "Ko kaɗan yallaɓai,idan har tayi tunani zata gane baka cutar da itaba, kuma Allah yaga niyyarka, kayi hakan ne dan kare martabarta da kiyaye hakkin Allah, amma yallaɓai mai zai hana kasanar da ita abinda ke faruwa ,dan gudun samun matsala nan gaba"tareeƙ ya faɗa yana mai kallon ogan nashi . Shiru Adeeb yayi na kusan minti biyu kafin yace" no tareeƙ ,she's too young ace munyi wannan maganar da ita,is better mubar maganar atsaninmu har zuwa lokacin da Allah zai bayyana iyayenta,inyaso saina basu ita ahannunsa,sannan kaga tayi free . "Shikenan yallaɓai amma yanzu kana ganin ,zaka kaita can gidane,ko kuma zata zauna anan?"tareeƙ ya faɗa yana kallon Adeeb da jiran jin me zaice. Kusan minti biyu Adeeb ya ɗauka kafin yace" ko zamanta anan tare dani akwai matsala tareeƙ bana so wataran zuciya ta Kani ga aikata wani abun da zai zamo na cutar da ita,zan kaita can gida gurin ammi ne tunda nima mafi zama can din" ya faɗa yana mai lumshe idanunsa. " Hakan yayi yallaɓai, Allah ya baka nasara akan kudirinka na alkairi" tareeƙ ya faɗa cike da ƙaunar ogannasa. "Ameen "Adeeb ya amsa ahankali tare da kwanciya. Ita kuwa wannan matar mai make up,kasancewar tareeƙ yayi mata bayanin komai tun kafin su zo gidan,dan haka da sallama tashi ga cikin dakin,juyowa fattu tayi da sauri tana kallon matar. Murmushi matar tayi tare da kama hannun fattu ta miƙar da ita tsaye tana murmushi, Kallonta kawai fattu keyi cikin tsoro da rashin sanin ko itaɗin wacece? Cikin harshen larabci matar ke cewa" kai masha Allah yarinya mai kyau da daukar hankali,gaskiya kina da sihirtaccen kyau,ƴata, zanyi Mali kwalliya mai kyau kamar ke" ta kai karshen magannarta tana murmushi. ita dai fattu kallon matar take tana tunanin wannan ɗin kuma daga ina ?wacece?kodai itace hulwar? Ahankali matar ta kama fattu ta zaunar da ita bakin gadon,gashin fattu ta fara warwarewa, " kai masha Allah,kina da gashi mai tsananin kyau,samun irin gashinki ba kowacce mace ba,larabawan ma" matar ta faɗa cikin harshen labarci, Ita dai fattu tayi gurum cike da tsoron matar,gashi kuma ta kasa koda yunƙurin gudawa ne bare ta tsere.haka matar ta kama fattu sukaje toilet ta wanke mata kanta tass,sanann suka fito. Gaban madubi ta kai fattu tare da ɗauki handryer ta busar da kan na fattu,mayuka kala-kala ta shafawa fattu akanta,kan kame tuni kan fattu ya ɗauki wani sheki da ƙamshi, ita kanta fattu wani sawai takejin kan nata. Gyara mata kan tayi sosai sannan ta ɗaure mata shi da wani ƙaton ribom mai kyau. Kwalliya tayiwa fattu cikin nutsuwa ba mai yawa ba,daga powder sai lips da kwalli ta sawa fattu a idonta,irin sakun nan da larabawa keyi,kusan rabin ido. Kai fattu fa tayi mugun kyau fuskar nan Tata kamar farin wata dan haske,kwalliyar ta karbi fuskarta sosai,kodan ba tabayin kwalliyar tayi ba oho? Ledojin nan mata ta buɗe tare da ɗauko wata bakar doguwar riga,dama kuma kayan duk dogayen riguna ne masu kyau da sutura jiki. Har zata dauko su bra,sai taga wata akan gadon ,dan haka sai bata daukoba. Wani ƙaton towel ta ɗauko ,dake gefen kofar bandakin asaƙale ,mikawa fattu tayi tare da cewa ta cire kayan jikinta ,saita sanya bra ɗin sannan tasa kayan nan.cikin harshen larabci matar ke magana.dan bata san cewa fattu bata jin larabci ba,dan kuwa ita tayi tunanin fattun ƴar Misran ce itama. Kallon fattu tayi gurum! Kamar kurma,dan bata san me matar ke faɗi ba.ganin fattu bata karɓi towel ɗin ba tana zaune kawai yasa matar tunanin kodai kurmace? Kwatance ta farayiwa fattu da hannu,cikin ikon Allah kuwa fattu ta gane wai rigar zata cire ta ɗaura towel din .karɓa fattu tayi tare da daura towel din asaman ƙirjinta.murmushi matar tayi tare da ɗaukar bra ɗin ta mikawa fattu.kallon brar fattu tayi tare da kallon matar" tab Ni nasan me zanyi da wannan abun da kina wani mikomin" fattu ta faɗa cikin ranta tana mai turo baki tare da kauda kanta. Murmushin matar tayi tana mai rayawa aranta ,kodai fattun kunyar saka bra ɗin take?dan ga dukkan alamu wannan ne karonta na farko asaka bra ɗin. Cikin hikima da dabara matar ta sakawa fattu bra bayan sun sha artabu,dan fattu sam ƙin yarda tayi da farko, aganinta wannan hulwar so take ta gane mata abubuwa,amma cikin hikima matar tayiwa fattu munin ba ganin jikinta zatayi ba tana son rufe mata jikinta ne,sannan ta dagawa fattu rigar jikinta tare da nuna mata itama ta saka irinta.sai lokacin fattu ta fahimci inda ake saka bra ɗin.ikon Allah wato suma waɗannan abubuwan harda jakar da ake boyewa?lallai zakaga abu da yawa idan baka mutuba. Aikuwa tsif bra din tayiwa fattu ajikinta,Dan dama koda tareeƙ yaje karbowa cewa yayi budurwa yar kimanin 16 za'a haɗawa kayan, Saidai fanties ɗin duk sun mata kaɗan sosai,da gyar matar ta samo mata wani mai kama da gajeren wando sannan tasaka. Da kanta ta sanya rigar ajikinta,masha Allah masu karatu duk wanda yaga fattu awannan lokacin zaiyi tunani wata fattun aka sake,dan tayi kyau har ta gaji da yin kyan. Tauraruwa matar ta fadawa fattu ajikinta masu daɗin ƙamshi,sannan tayi mata rolling ta ɓame da wani kyakykyawan abinda ake riƙe mayafi dashi dan gudun zamewa. Sosai matar ke yaba kyan da Fattun tayi , ga sarƙarta sai walwala take,matar sai kallon sakar take cike da jinjina irin kuɗin da aka batar wajen siyanta,kafin ta kama hannun fattun ta juya da ita gaban madubi.saida gaban fattu ya faɗilokacin datayi arba da kyakyakywar fuskarta jikin madubi,hannu tasa tare da shafa fuskartata,dan tabbatarwa itaɗince kuwa. Ƙuri!! Fattu ta kure kanta da kallo ta jikin madubi,wai dama haka take ko kuma dai ba ita bace wannan ɗin?anya matar nan ba sake mata fuska tayi ba ?dan dan ita bataga tsohuwar fuskarta ta da ajikin madubin ba. Murmushin tayi lokacin data ɗan mintsini hannunta kadan,kuma taji zafi. Wllh nice ,nice fattun baffa, gaba daya na zama ƴar gayu aradu zan tsula tsiya, wayyo Allah na ,ina Hamma yazo ya ganni ,yaga yadda na koma fattu ƴar gayu. Juyowa fattu tayi tana kallon matar nan, fuskarta dauke da murmushi, itama matar murmushin tayi tana yaba kyau da Allah ya ba faytu. Wayar matar ce tayi ƙara hakan yasa ta dauka ba tare da tace komai ba ta kara akunnenta, "To yallaɓai ganin nan" Shine abinda matar ta faɗa tana mai haɗa jakarta ,sallama tayi fattu bayan ta rungume fattun. Koda matar ta fita tsayawa fattu tayi jikin madubin nan tana ƙara kallon kanta,tajita nan ta juya can tana dariya ƙasa -ƙasa. Adeeb ne ya shigo ɗakin sanye da farar jallabiya mai tsananin kyau da ɗaukar ido,kansa kuma hiramine sai wannan baƙin abun da suke ɗorawa asaman hiramin, ba ƙaramin kyau yayi ba sai sheƙi fuskarsa keyi. Tsak !ya tsaya abakin ƙofar yana mai faɗin "masha Allah,watabarakallahu fi ahsanil kaliƙin" lokacin da yayi arba da ƴar gayu fattu,wacce Bama tasan yana gurin ba,kallon kanta kawai take ,ta taɓa nan ta taɓa can. Saida yayi gama ƙureta da kallo,yaga dai idan ya biye ta kallonta to zasu kwana anan ba tare da ya gaji da kallon nata ba,dan haka sai yayi ɗan gyaran murya kafin yace " idan kin gama kalle madubin zo mutafi. Sai lokacin fattu ta an kare da Hammana nata na gurin" cikin jin daɗi ta nufeshi tana murmushi," Hamma kalli yadda matar nan ta sauya min fuska? Wllh gani nake kamar bani ba "fattu ta faɗa tana dariyarta mai burge wa da ban sha'awa. Kallonta kawai Adeeb yake ,dan shikam ya rasa bakin magana ma,gaba ɗaya fattu ta sanya shi cikin wani yanayi na ruɗewa da zallar kyanta. Ita kuwa tana tsaye gabansa sai rangaji take ,jinta take kamar sarauniya yau ɗin nan. Ahankali Adeeb ya kai kallonsa kan waɗan nan abubuwan na fattu, ajiyar zuciya ya sauke ganin yanzu kam ta saka wannan abar.dan haka hannunta kawai ya kamo sukayi waje. Sai lokacin fattu ta sami damar kallon tsarin falon,sama gidan baki ɗaya . Suna tafe amma fattu na waige waige,ikon Allah Allah garin daɗi na nesa,ashe su amaƙabarta suke,anya kuwa wannan gidan ba aljannar duniya bane.ahankali tace " kaikuwa Hamma dan Allah wannan gidan na waye?"ta faɗa tana kallon yadda yake danna nonbibin bude ƙofar. Kallonta yayi bayan sun fito farfajiyar gidan,kafin ahankali yace "nawa ne" Baki fattu ta buɗe cike da mamaki kafin tace " ikon Allah, to Hamma a ina ka sami kudin gina wannan gidan, dan nasan aradu zai kai kusan dubu saba'in ko tamanin " ta faɗa tana irin jinjina kan nan na ta kwaso kudi da yawa. Dariya ce ma ta kama Adeeb ,saidai kasancewarsa ba mai yawan dariya ba yasa yayi murmushi kawai ,kafin yace " ki tara kuɗin da kika faɗa kibani na baki gidan" ya faɗa cikin nishadi,haka kawai yake jinsa cikin wani irin nishaɗi dajin daɗi Kama baki fattu tayi cikin zato ido tace"woooooh Ni ɗiyar baffa,ina zanga wannan uban kuɗaɗen? saidai idan kaina san siyar insamu, Ni wllh bazan gina gida irin wannan ba ma,haba saikace wanda zan zauna da aljanun duniya acikin" ta faɗa tana wani dan taɓe baki irinna rufamin ashirin nan. Kallonta Adeeb ya ɗanyi, yadda take ta zuba masa surutu,ashe dama tana da surutu haka?yanzu ta sake dashi sosai,kuma ya fuskanci idan suna tare sam bata fiye lura da wasu abubuwan da zata gani taji tsoroba. Dai dai nan suka kawo wajen ajiye motoci,kafin su karasa saiga tareeƙ ya fito daga cikin wata rantsatstsiyar mota Black,mai baƙin gilasai,motace yar ubansu wacce kana gani kasan anyi barin kuɗin agurinta. Bude musu motar yayi yana ɗan satar kallon fattu,wai zuƙi haka yarinyar take dama,gaskiya yana fatan Allah yasa wanan alherin da suka ƙalla karya kunce . Harararta Adeeb yayi cikin jin haushi yadda ya kafawa fattu idanu yace " to yi da gaske ka cinyeta" ya faɗa cikin harshen larabci yana hararar tareeƙ . Dan sosa kai tareeƙ yayi yana murmushi,azuciyarsa yana faɗin lallai yallaɓai irin wannan kishi haka kiri-ƙiri?hmmmmm . Shiga motar sukayi fattu na ta kallon yadda motar take wani sukuf da ita ,kamar siffar wani kwaron, Kallon Adeeb tayi wanda ya jingina kansa da jikin kujera as usual idanunsa alumshe. "Hamma wai a wannan duniyar da mukazo, acikin kwarya ake yawo ne?"ta faɗa tana mai riƙe haɓa. Idonsa daya ya buɗe tare da kallon ta ,yana rasa mai zai ce mata dan takaice wai motace ƙwaro,kai fattu sai gyaran Allah. Ganin yayi shiru ta kuma cewa "Hamma yanzu kuma wace duniyar zamu?" Kai Adeeb ya dafe cike da gajiya surutu yace " duniyar cinye mutane masu surutu" ya faɗa yana harararta. Allah Sarki fattu dagalo!!tayi tana kallonsa cikin mutuwar jiki ,kafin ahankali ta ɗan matsa kusa dashi tare da kamo hannun rigarsa ta rike tayi kalar tausayi sosai ,ashe duk murnar da take dama duniyar cinye mutane zasu koma,?shikenan bazata ƙara ganin baffanta ba? Ahankali tace "Hamma baffa.... "Hihhhhhhhh" Adeeb ya fada yana mai ɗora danyatsarsa akan bakin fattu,sannan ya kwanto da kanta zuwa kafaɗarsa. Kwanciya tayi lamo cike da tunani kala kala aranta . Tafiya sukayi mai ɗan nisa kafin naga sunzo gaban wani irin makeken gida mai matukar girma da ƙasa,girman gidan yayi haɗa anguwanni manya guda uku,get suka nufa ,suna idan akaga tareeƙ sai abude masa cikin girmamawa,ba wanda ya kula da Adeeb dake bayan motar,dan glass ɗin bakinsa sosai. Saida suka wuce manyan get bakwai ,kafin suka nufi wani get mai matukar kyau da girma,wani irin walwali get ɗin keyi kai kace da zallar kwal akayishi. Daga samansa kuma wasu danjojine masu ruwan kwal ke rubuta, Well come to the King palace cikin manyan baki. Ahankali get din ya buɗe bayan wata doguwar na'ura ta danno kai ta haske ko ina cikin motar . "Yallaɓai mun karaso" tareeƙ ya faɗa yana ɗan juyowa kadan. Shiru Adeeb yayi yana mai jin wani irin kewa da damuwa azuciyarsa." Tareeƙ how long na dauka ba'asan inda nake ba?Adeeb ya tambaya cikin sanyin murya. "Yallaɓai 5 months 3days" tareeƙ ya faɗa cikin jimami. Runtse idanu Adeeb yayi tare da budewa ,da sauri kuma ya yunƙura tare da dauke kan fattu daga kafaɗunsa,wacce tayi lamo kamar mai barci tsoro duk ya gama cika mata ciki. Fitowa yayi daga motar kafin ya fara takawa cikin nutsuwa da jin kewar iyayensa. Da sauri fattu ta fito daga mota ita ta riga da gudu tabi bayan Adeeb,Allah yasa flat shoe ne akafarta.saurin kamo gefen hiraminsa tayi ta riƙe gan cikin hannunta.yana jinta baice mata komai ba ,har suka kai bakin ƙofar. Ahankali ya nuna fuskarsa jikin wani dan madubi,wani dogon layine naga yana zagaye fuskar tashi,kafin kofar ta buɗe da kanta,yana sanya kafa cikin wani tafkeken falo ,naji wata murya ta dauki Magana," Well come home prince Adeeb Muhammad Ashraf ,your hinest you have a big surprise to see " Masu karatu fattu fa gaba ɗaya ta tsure da ganin irin duniyar da suka shigo,wani irin mahaukacin falone ,wanda ta ko ina matsalar benece acikinsa, ga wani dan banzan sanyi da ƙamshi dake dukan hancin ta.nan da nan jikinta ya kama rawa. Ta rike hannun Adeeb gam-gam cikin nata. Kamo hannun nata yayi tare da kanta zuwa cikin tsakiyar falon,wanda da gyar fattu ke taka ƙafarta dan wani irin kaishi da taji a ƙasa dakin. Zaunar da ita yayi yana mai kallonta, "Ki zauna anan, za'a shigo dake yanzu." Adeeb ya faɗa yana mai kallon yadda jikinta ke tsuma. Hannunsa ta kara damkewa kafin tace "Hamma tsoro nakeji sosai" ta faɗa cikin rawar murya. Hannun nata ya kama ahankali ya kai bakinsa ya sunbata, kafin ya shafa gefen fuskarta ,yace kijirani kinji " yana faɗin haka yabi matakalar dake tsakiyar falon yayi sama. Kallo fattu tabishi dashi cike da tsantsar tsoron wannan guri.hawayene ya zubo mata sharrrrr!! Daga idanunta,ahankali ta sanya hannu ta share wahayen . Shikuwa Adeeb wani haɗaɗden part ɗin naga ya nufa asaman,hadimaine birjik farfajiyar gurin kowa da abinda yake ,tafiya yake cikin sauri da sassafar,ba abinda yake so da buri illa yayi ido hudu da abinsa.wata baiwa ce ta ankare da Adeeb,cikin hanzari ta zube ƙasa tana faɗin Takawarka lafiya ,dan sarki jikan sarki,yarima mai jiran gado,alherin Allah ya kai maka. Da sauri duka suka ankare da abinda baiwar nanke fadi,cikin azama da tsantsar farin ciki sauran ma suka zube ƙasa suna kwasar gaisu da murnar ganin Adeeb,ba wanda Adeeb ya kula kai tsaye dakin mahaifinsa ya nufa. Ahankali ya buɗe kofar cikin sanyin murya yayi sallama. Wani farin Balarabe dattijone kwance akan wani lafiyayyen gado irin na sarakuna masu ji da kansu,gefensa kuma wani likita ne ke ƙoƙarin daura masa ruwa ahannunsa, Sai wani mata guda biyu dattijai, sunsha ado da gwala-gwalai na alfarma ,ko wacce tana inbakiyi bani guri, Sai wani farin matashi zaune kusa da dattijon nan,ya riƙe hannunsa. Cikin azama dattijon ya wani zabura tare da sauƙowa daga kan gadon yana mai goge idanunsa,kafin cikin rawar murya yace " habeebee Adeeb " Ya faɗa tana nuna gofar dakin ,inda Adeeb ke tsaye ,cikin shaukin ganin mahaifin nashi. Gaba dayan yan dakin ne suka biyo suna kallon ƙofar dakin,aikuwa Adeeb ne ya dawo,prince Adeeb ya dawo gida. Da gudu Adeeb ya karaso cikin dakin tare da rungume dattijon nan ajikinsa tsantsan yana mai faɗin," habeebe rurh cikin kuka" Shima kuka kawai dattijon nan yasa tare da ƙanƙame Adeeb ajikinsa. Matan nan kuwa kallon kallo naga sun fara cikin rudewa da shiga kokwanto. Masu karatu muje zuwa yau dai ga fattu cikin gidan sarautar Masar,koya zata kasance? Ga kuma Adeeb jikin mahaifinsa . Sai mun hade next page. Anty mammynku ce Mrs babi💘💘💘 Share and comment fisabilillah More comment More typing. [7/24, 3:05 PM] Abue Saleh AlQuyraemey: 🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄 MACIJI NE🪱🪱🪱 Na mammy kabeer (Anty mammy) Elegant online writers📚📚 Free book Page 35/36 _______________Kallon- kallo naga matan nan nayi atsakaninsu, ko wacce tana jifar ƴar uwarta da mugun kallo, yayi da zuciyoyinsu ke buga cike da mamaki . " Habeebee ina kashiga? Me yasami rayuwarka? Na shiga damu matuƙa lokacin da muka wayi gari an nemeka anrasa ba ƙasashen da bamu zagaye ba wajen nemanka, na sanya ƙudede, kadarori,dama kanfanunuwa na ga duk wanda ya kawo min koda labarin in da kake ne,amma bamu sami komai da ya shafeka ba,meke faruwa habeebee?"dattijon nan ya faɗa yana mai shafa fuskar Adeeb hawaye na zuba daga idanunsa. Ahankali Adeeb ya kamo hannun mahaifin nashi ,tare da sumbatar hannunsa ,sannan yace " abie wasu abubuwan basu buƙatar afadesu,saidai kawai mubarsu cikin zuciyarmu, sannan muyi ta kallon azzaluman dake neman ganin bayanmu da bakin halinsu." Adeeb ya faɗa yana mai kallon daya daga cikin matan dake tsaye aɗakin. Kallone irin na duk abinda kike aikatawa akaina, na sani kuma ki kiyaye ranar haduwarmu. Ahankali naga matar cikin ruɗewa da irin kallon da Adeeb ke mata,ta sanya gefen mayafin dake kanta tana goge zufa daga goshinta ,kanta a ƙasa. Ita kuwa ɗayar mata cikin sassarfa ta karaso gaban Adeeb ,hannu tasa akan kumatunsa tana shafawa, hawaye ya gama wanke mata fuska. "Hayatee nayi kewarka fiye da yadda zan fadamaka, naji daɗi da Allah ya kuɓutar dakai daga sharrin mahassada" matar ta faɗa cikin kuka tana mai rungume Adeeb. " Ammina" Adeeb ya faɗa cikin wata irin murya mai cike da kewa ,yana mai rungume matar daya kira da amminsa. Matashinnan kuwa gaba daya ya haɗe fuska ,ba alamun fara'a ko murnar dawowar Adeeb gida atare dashi.zamu iya cewa ma bakin ciki yake da ganin Adeeb ɗin. Zama sukayi abakin gadon ,shida mahaifin nashi,fuskokinsu dauke da mafificin farin ciki da ɗauki ganin juna. " Habeebee ka bani labarin abinda ya faru" mahaifinsa ya faɗa yana mai kwantar da kan Adeeb ɗin akan cinyarsa. Kwanciya Adeeb yayi tare da kamo hannun mahaifin nashi kafin yace " abie ,zan baka labarin komai daya sameni ,amma yanzu baka da lafiya ka huta kayi barci abie na" Adeeb ya faɗa yana sumbatar hannun mahaifin nashi. Dariyar farin ciki abie yayi tare da shafa kan Adeeb yace " ai naji sauki yanzu kam ,wanda yayi silar kamuwa da cutar yazo ya bani magani,bana jin ciwon komai habeebee likita ,zaka iya tafiya" abie ya faɗa yana mai kallon likitan cikin fara'a . Godiya likitan yayi cikin garmamawa ,yana mai taya sarki murnar dawowar Adeeb ɗin gida,dan kowa yasan da batun bacewar Adeeb ɗin. Dubawa nayi cikin dakin naga ya rage daga sarki sai Adeeb da ammi,amma ɗayar matar da saurayin nan tuni sun bar ɗakin. Fattu kuwa tana nan zaune afalon wannan matar ta sauko daga saman sarki cikin wani irin yanayi ,dan ko lura da fattu batayi ba, sai ƙoƙarin kiran waya take . Ba jimawa kuma,saiga wannan kyakyakywan saurayin shima ya fito cikin fushi da bacin rai,kallonsa fattu keyi taba dan hango yanayin kama da sukayi da Adeeb,saidai ko kama ƙafar kyan Adeeb baiyi ba. Harya gota inda fattu ke zaune ,sai kuma ya dawo da sauri ya tsaya akanta. Fattu kuwa da sauri ta mike tsaye tana kallonsa.ganin irin yadda ya tsaya mata akai ƙerere. Shikuwa saurayin nan mai suna,Rashad ,wani irin. Shegen kallo yake bin fattu dashi,tunda ga sama har kasa,wow wannan kayan fa ?daga ina haka?ya faɗa cikin zuciyarsa yana mai kashewa fattu idanu. Haɗe fuska fattu tayi tana mai turo baki tare da kawar da kanta gefe. "Hi babe !" Rashad ya faɗa yana mai ƙoƙarin kamo hannun fattu. Da sauri fattu tayi baya tana mai turo baki tare da biye hannunta abayanta. Murmushin gefen baki yayi tare da shafa gefen fuskar fattu yace " yanzu ina cikin hanzari amma zan nemeki,dan kin kwanta araina kuma yawuna ya tsinke" ya faɗa yana mai wucewa bayan ya sunbaci hannun daya taɓa fuskar fattu dashi. Duk zancen da yake da larabci yake yinsa,dan haka ba abinda fattu ta fahimta cikin zancen nasa.taɓe baki tayi tare da binsa da harara , tana faɗin" Allah ya isa taɓa min fuska da kayi" ta faɗa afili tana mai murguda baki,sannan ta koma ta zauna. Tana nan zaune shiru -shiru agurin nan ,tunanin take ko ina Hamma ya shiga ya barta anan?karfa taje tana zaune kawai taji anfara yankan naman jikinta,ga shegen sanyin falon duk ya isheta. Wani irin ƙamshine ya doki hancin fattu,cikin sauri ta lumshe idanunta tare da budewa tana mai kallon ta inda tajiyo ƙamshin, Masha Allah,wata kyakyakywar budurwace mai tsananin kyau da gayu,taci ado da wata doguwar riga baƙa ,mai tsayin gaske ,dan saida wasu yammata kusa su shida dake Binta abaya suka riƙe kasan rigar,gaba daya wuyanta da hannunta hatta gashin kanta anyi masa ado ne da kwal,tayi kyau matukar gaske,kallo daya zakayi mata kasan tana cikin farin ciki,dan kuwa sai murmushi take,tana tafiya ɗas-ɗas cikin salo da yanga. Kallonta kawai fattu keyi cike da tunanin wannan ɗin ko wacece?amma gaskiya ƴar gayuce ta gaske,nima nan gaba irin wannan kwalliyar zan riƙayi inji ta yanga abina.fattu ta faɗa cike da murmushi tana kallon budurwar. Ita kuwa budurwa tana karasowa tsakiyar falon ,idonta ya sauƙa akan fattu,dammmm !taji gabanta ya faɗi, wannan ɗin kuma wacece?daga ina haka?me takeyi acikin babban falo?budurwar ta faɗa cikin zuciyarta ,tana mai jin wani irin tsabar fattu cikin zuciyarta,dan saitaga duk yadda take taƙama da kyau wannan yarinyar tafita,saidai kawai tafi wannan wayewa da sanin duniya. Kallon -kallo aka fara tsakanin fattu da wannan budurwa,ba abinda ya ƙara batawa budurwar nan rai irin yadda fattu ta tsareta da ido,wato ko shakkar ta ma batayi. Cikin takunta na isa da rangwada ta ƙarasa gurin da Fattun ke zaune, Kallon wulaƙanci take yiwa fattu tana wani yamutse fuska. " Wacece ke? Budurwar ta faɗa cikin harshen larabci. Kallonta fattu tayi ba tare da tace komai ba,dan bata san me take cewa ba. Ran budurwar ne ya ɓaci sosai,hannu tasa tare da fizgo fattu ta kama kwalar rigarta, cikin isa da gadara take faɗin" ke kinsan komi wacece ina miki magana kika shareni?ke ƴar uban waye marar kunya?"budurwar ta sake faɗa cikin fushi, Fattu kuwa cikin jin zafin abinda budurwar tayi mata ta ballawa budurwar harara tare da ture hannun budurwar daga wuyanta,tana mai murguda baki. Gaba daya hadiman da suka taki budurwar nan zato ido sukayi,cikin tsoro da tausaya wa fattu ,dan ta tabka babban kuskure. Zato ido budurwar tayi itama tana mai kallon fattu ," kee!!! Ni kika turewa hannu?lallai minti babban kuskure.budurwar ta faɗa tana mai ɗauke fattu da wani lafiyayyen mari, kafin fattu da gama dawowa cikin hayyacinta ta sake jin wani zazzafan marin a dayan kumatunta. Wani irin azabar raɗaɗine ya ziyarci fuskar fattu,cikin hanzari ta dafe duka kumatunta tana kallon budurwar nan,nan da nan zuciyar ƴaƴan Fulani ta motsowa fattu, ai batasan lokacin data ɗaga hannu itama ta shararawa budurwar nan matuka har biyu ba....... Manage please my fans, Wllh am seek. Mrs babi ce💘💘💘 [7/25, 6:57 PM] Aishat Anty: 🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄 MACIJI NE🪱🪱🪱 Na mammy kabeer (anty mammy) Elegant online writers📚📚 Free book Page 37/38 https://facebook.com/groups/943534712916776/ Masu amfani da Facebook sai kuyi join wan nan link din ________________cike da zallar madarar mamaki budurwar nan ke kallon fattu,tunda take arayuwarta ba wani mahaluƙin daya taɓa daga hannu da sunann ya faɗa mata koda baƙar magana ne, amma wai yau itace tsaye gaban wata kucakar yarinya,sannan agaban bayinta ,dafe da kunci,wai da sunan an sharara mata maruka har biyu? Lallai wannan yau ko ƴar gidan uban waye saita gane kurenta, zata san cewa ni Zulaihat nafi ƙarfin awulaƙantani ,kuma azauna lafiya. Gaba ɗaya barorin gimbiya Zulaihat atsorace suke ,kuma kawunansu sunkuye a ƙasa, yayin da zuciyoyinsu ke bugawa cikin tsoro da fargabar abinda zai biyo baya. Fattu kuwa tana tsaye riƙe da ƙugu,ta ƙurawa gimbiya Zulaihat idanu,kamar yadda itama ke kallon fattun,lokaci ɗaya fattu taji mugun tsabar Zulaihat cikin zuciyarta,haka kawai zata wani daga hannu ta dallamin uban mari?ai wllh saidai acinyeni agidan nan,amma idan wannan banzar tayi min abu saina rama dan ba tsoronta nakeji ba ehe.fattu ke wannan zancen ,cikin zuciyarta tare da murguda baki bayan ta kammala zancen zucinta. H Ahargitse gimbiya Zulaihat ta fara juye-juye ,can ta hango wani ƙarin flower vase na tangaran,da hanzari tayi gurin da tare da rarumoshi tayi kan fattu tana huci. Tsorone ya gama kama fattu,yanzu idan ta jibga mata wannan ƙaton abun akai ,ai wllh sai kanta yayi raga-raga,tab yaseen bazata tsaya ba.baya fattu ta farayi cikin tsoro tana mai kallon gimbiya Zulaihat, Ita kuwa gimbiya zulaihat ganin fattu na ƙoƙarin gudawa yasa ta dakawa hadimanta tsawa akan su riƙe mata fattu,wani irin zafi takeji cikin zuciyarta,wllh zata iya kashe fattu yadda takejin tsanar fattun cikin ranta,dan haka tayi rantsuwa yau saita illata fattu,ta yadda ko hannunta bazai ƙara moruwa ba,bare ta sake gigin marin wani. Cikin azama kuwa suka tsakumi fattu suka riƙe ta,ihu fattu ta fara cike da tsoron abinda matar nan zata mata," wayyo Allah na Hamma kazo, zasu cinyeni danya da raina ,wayyo hammana!wayyo Hamma kana ina!! Fattu ta faɗa cikin ihu,lokacin da tajita ahannun waɗannan manyan yan matan masu shegen ƙarfi. Zulaihat kuwa cikin rashin imani da tsana take faɗin,"wllh yau saikin komi wacece ,kin siya babban kuskuren taɓa Zulaihat,kuma yau zaki girbi abinda kika shuka" Zulaihat ta faɗa cikin fushi tana daga wannan flower vase ɗin da iya ƙarfi ta zata sakarwa fattu. "Zulaihaaaatttttt!!!!" Aka kwalla kiran sunan gimbiya Zulaihat din ,cikin wani irin sauti mai ƙarfin gaske ,wanda saida dukansu suka tsorata . Afirgice Zulaihat ta saki flower vase ɗin nan daga hannunta ya fadi ƙasa. Ba kowa bane yayi mata wannan bahagon kiran face Adeeb ,wanda ya fito ne dan shigowa da fattu gurin mai martaba,lokacin ya gama basu labarin irin taimakon da fattu da baffanta sukayi masa ,da kuma dalilin tahowa da ita nan ɗin .shine mai martaba yace ya shigo da ita ciki. Dama kuma yana zaune ne ,amma zuciyarsa tana can gurin fattu,dan yasan ta da shegen tsoro,abu kaɗan ne zai firgitata. Dan haka cikin sauri yake tafi lokacin daya fito daga part ɗin sarki, Yana doso babban farko kuwa ya fara jin ihuj fattu tana kiran sunansa.dan haka da gudunsa ya ƙaraso cikin falon,yana zuwa idanunsa sukayi masa mummunan gani,Zulaihat na ƙoƙarin illata masa Hulwa. Cike da tsoro bayin nan suka saki fattu tare da zubewa kasa suna gaida Adeeb. Wani shegen kallo da Adeeb ya watsa musune yasasu ficewa daga falon da gudu cike da tsantsar tsoro . Fattu kuwa da gudu ta nufi Adeeb tana kuka,cikin sauri shima yake saukowa daga matakalar benen, uku -uku,hurhuɗu yake tsallake step din, atsakiya falon suka hade da fattu,tana zuwa ta faɗa ƙirjinsa tare da ƙanƙame shi tana kuka."Hamma mutafi daga gidan nan,tsoro nakeji,wannan matar muguwace daga zuwa ta ta mareni har sau biyu,kuma tasa wadancan doyoyin suka rikeni wai zata baremin kai" fattu ke faɗin haka cikin kuka tana kwance akan ƙirjin Adeeb. Wani irin tausayin fattu ne yake mamaye ilahirin jikin Adeeb,tare da tsantsar jin haushin Zulaihat cikin ransa. Ahankali yake shafa bayan fattu yana shiiiiiiiii da bakinsa alamun rarrashi. Idanunsa sun kada sunyi mugun jaaaa ya kafesu akan fuskar Zulaihat,wacce tayi mutuwar tsaye tana kallon wannan yarinyar kwance akan ƙirjin Adeeb,wanda ita bata taɓa samun wannan damar ba.banda bugawa ba abinda zuciyarta keyi,lallai akwai gagarumar matsala,wacece wannan yarinyar?meye alaƙarta da Adeeb? Cikin daukewar tunani da tsananin kishi daya rufewazulaihat idanu,kunsan matan larabawa da bakin kishi,Zulaihat ta nufi kansu Adeeb gadan -gadan.tana zuwa ta sanya hannu tare da ƙoƙarin fizge fattu daga jikin Adeeb. Wasu zafafan marukane guda biyu suka sami gurbin zama akan fuskar Zulaihat ɗin,wanda sun fitowa daga hannun Adeeb. Kusan minti biyu Zulaihat ta dauka kafin ji da ganinta sudawo daidai. Ihu ta kurma cikin azaba tana mai dafe kumatunta" habeebee nika mara?akan wannan jakar?wacece ita?meye alaƙarka da ita ? Da har zata kwanta akan ƙirjinsa,kaikuwa kana rarrashinta?Zulaihat ta faɗa cikin kuka da rikicewa. Wani matsiyacin kallo Adeeb yayi mata, yana mai gyarawa fattu kwanciyarta akan ƙirjinsa kafin yace " ita ɗin mutumce mai matukar muhimmanci arayuwata,mafi kusanci da zuciyata wacce zan iya aikata komai akanta,ki kiyaye nan gaba,hukuncin da zan miki bazaiyiwa kowa daɗi ba " Adeeb ya faɗa cikin wata iriyar murya mai kama da ta basasa,yana mai nuna Zulaihat da hannunsa. Cikin karawa kukanta ƙarfi Zulaihat tace" kana nufin harni,tafini muhimmanci agareka?" Ta faɗa cikin ruɗu. Wani banzan kallo Adeeb ya wurgawa Zulaihat kafin yace " ke wacece?wane matsayi kike dashi agareni,karki ƙara haɗa kanki da Hulwa banza shashasha marar zuciya da kamun kai " Adeeb ya fada yana mai juyawa da fattu suka fara tafiya zuwa sama. Cikin kuka kamar zata shiɗe Zulaihat tace " wacece ita" Saida sukayi taku kusan uku ,kafin Adeeb ya juyo cikin murtukakkiyar fuskarsa yace " MATA TACE ita" ya faɗa yana mai tsare Zulaihat da idanu. Wani wasan ihu Zulaihat ta kwalla tare da ficewa da gudu ta nufi waje. Harara Adeeb ya bita dashi kafin ya juya suka ci gaba da tafiya ,duk abinda suka faɗa fattu batasani ba, dan da Yaren larabci sukayi maganarsu. Saida sukaje bakin ƙofar part ɗin sarki sannan Adeeb ya tsaya tare da gogewa fattu hawayenta.yace "kinga duk kin bata kwalliyarki da hawaye, kiyi shiru zamuje gurin abie ne yanzu kinji?karki damu bazata ƙara yi miki komai ba"ya faɗa yana mai riƙe kumatunta. Kallonsa fattu keyi tare da shagwabe fuska tace " Hamma Ni tsoro nakeji" "Ba abinda zai sameki ,bagani ba?" Ya faɗa yana kama hannunta suka shiga dakin abie. Zulaihat kuwa tana ficewa daga falon,kai tsaye mota taje ta shiga tana kuka kamar ranta zai fice,da mugun gudu take tafiya hatta bar cikin masarautar ,kai tsaye wani hotel ta nufa tana zuwa dama akwai dakin dake amazaunin nata cikin hotel ɗin. Fridge ta buɗe tare da ɗauko wata kwalba ta buɗe cikin sauri tare da kafa kai ,saida ta shanye abinda ke ciki tass kafin ta jefar da kwalbar. Waya ta dauka tare da kiran wata number tace tana jira. Ko minti biyar ba'ayin saiga wani saurayi kyakyakywa ya shigo ɗakin ,yana zuwa lokacin harta fara fita daga hayyacinta ,tana surutai," saina kasheta ,saina ranta da yarimana ,nawa ne Ni kadai. Rungume saurayin tayi suka fara aikata alfasharsu,subhanallah,Zulaihat Allah ya shirya. Adeeb kuwa suna shiga dakin abie ,fattu ta kama gefen rigarsa ta rike gan! Cikin hannunta .ammi ce ta ƙaraso tare da kamo hannun fattu tana murmushi tace "ƴata yar albarka sannu kinji" ammi ta faɗa tana mai rungume fattu. Abie ma murmushi taye yana mai kallon fattu ,lokaci ɗaya yaji yarinyar ta kwanta masa arai tana da hankali da nutsuwa. Nan ammi tace agurinta fattu zata zauna ,ita zata kula da ita ,sannan zata taya Adeeb cigiyar mahaifan fattun. Bayan sati guda Sarki ya hada wani gagarumin taro na farin cikin dawowar babban dansa magajin faɗa,wanda aka gayyato sarakuna daga kasashe daban -daban. Kuma nan da kwana biyu taron zai gudana,dan haka gyara ake yiwa masarautar sosai.ko ina ka kalla an gyara shi yayi mugun kyau, Adeeb kuwa shima yanzu ya shiga busy,yana ɗan bin kamfanoninsa na kasashe daban -daban yana duba yadda harkokin ke tafiya,dan haka yau kwana hudu baya gida .kuma basu hadu da fattu ba . Gaba ɗaya fattu ta shiga damuwa,kullum tana cikin dakinta da aka bata mai shehun kyau,saidai akawo mata abinci taci ,tayi wanka ta kwanta. Ko falo baya fita.itama ammi gaba ɗaya bata zama tana ta uzuri. Gashi bata ita tare su ba,Gara ammi wataran takan dan yi mata Hausa kadan kadan. Yau dai fattu tana zaune shiru ,tace bari ta fito falo dan yasan huta kuma ta duba Hammana. Tana sanye da doguwar riga milk mai fadi kanta yanke da mayafin rigar,ba kwalliya akan fuskarta amma tayi kyau sosai. Falon ta fito tana binsa da kallo,ya hadu iyakar hafuwa, sai ƙamshi ke tashi ta ko ina. Tana ɗan zagayenta afalon ,taji anbude kofa. Juyawa tayi ɗan ganin waye ya shigo, Rashad ne ya shigo ɗakin shida zulaihat.suna tafe suna dan magana ,da alama kuma rarraba jin Zulaihat ɗin yake. Turus suka tsaya suna kallon -kallo atsakaninsu su ukun. Ita dai fattu kallonsu take tana tunanin,dama wannan matar agidan nan take ?tun ranar bata sake ganinta ba,sannan Kuma ta gane wannan. Saurayin,shine wanda ya taba mata kumatu awancan ɗakin,dan haka da sauri fattu ta kawar da kanta gefe tare da hade fuska, nemar guri tayi ta zauna akan lumtsuma luntsuman kujerun da suka yiwa falon ƙawanya. "Kai !!Rashad me wannan fitsararriyar keyi anan?aikuwa wllh saina koya mata hankali"Zulaihat ta faɗa tana ƙoƙarin ƙarasawa kusa da fattu. Da sauri Rashad ya riko hannunta yana mai faɗin "haba -haba ke matsala ta dake gaggawa ,ba yanzu muka gama magana dake ba,zaki taimakeni,nima zan taimakeki, cikin sauƙin kowa ya sami abinda yake so. Idan kika yi wani abu yanzu ,to shirin mu ga zai wargaje,kuma kinsan wancan horon bashi da sauƙi ko kaɗan.ba dai jini ne za'ayi taron nan ba? Rashad ya faɗa yana mai sakin wani shegen murmushi. Jinjina kai Zulaihat tayi tana mai hararar fattu. Cigaba Rashad yayi da maganarsa"to ki kwantar da hankalinki, ranar zamu aiwatar da ƙudirinmu akanta ,zamu tarwatsa koma menene ke tsakaninsu,Ni sam na kasa gane inda ammi ta dosa ,bata bamu goyon baya kamar yadda ya kamata,amma zamuiyi komai da kanmu. Kedai kawai ki danne zuciyarki akan komai har zuwa jibin" Rashad ya faɗa cike da ƙarfafawa Zulaihat gwuiwa. Jinjina kai tayi cikin murmushi tace " nasanka nasan halinka,kuma zaka iya Allah ya nuna mana lokaci, amma wllh na tsani yarinyar nan sosai acikin raina" Zulaihat ta faɗa tana hararar fattu. Fattu kuwa murguda mata baki tayi itama tana mai cewa cikin ranta" oho dai saidai kiyi ta hararata amma wllh baki isa ki doke in gyaleki ba ,ba ruwana da wani kin girmeni ehe" fattu ta faɗa tana mai dan dukan cinyarta har saida ƙaran ya fito sukaji. Kallonta sukayi gaba dayansu ,Zulaihat tace ka "gani ko dukda batasan me muke cewa ba,amma kalli abinda take ?wllh daka barni na tattara yarinyar nan,ai Prince baya gida bare yace wani abu"Zulaihat ta faɗa cikin muryar bacin rai. "No karki fara,ko baya gida yanzu ai kinsan zai dawo ko?kuma ma gaskiya bazan bari ki taba min kayana ba,dan gaskiya ina hango hutu agurin man sosai " Rashad ya faɗa yana wani kashe ido tare da kallon fattu. " Wllh Ni haushi ma kake bani ,akan wannan kucakar zaka wani tsaya bata lokacinka,me zaka samu jikin wannan banzar?"cewar Zulaihat cikin haushi. " Ke wllh ƙarya kike kinsan wannan yarinyar tafiki komai na mata ,kalleta mana da kyau ki gani ,aikinsa ba karya ,malam komai yaji yadda ake bukata" cewar Rashad cikin wani irin shegen voice . Tsabar haushi daya kama Zulaihat tashi tayi afusace ta bar falon tana ƙunƙuni. Adeeb yana can ƙasar farin yana gudanar da binciken kasuwanci sa ,gefe guda kuma ya dage sosai wajen neman iyayen fattu,yasa hoton sarkar nan Tata da rigarta tare da nuna yana neman wanda yasan waɗan nan kayan,saidai bai yarda ya nuna wata alama da zata nuna shike neman wanda yasan wani abu game da kayan ba,dan nunawa yayi shidin talaka ne sosai . Kullum suna waya da ammi yana tambayarta fattu ,sannan yace ta rinƙa koya mata Yaren larabci ,kuma ammi tana kokarin koyawa fattun ,dan yau take son kawo tsohuwa salima ,ta zauna tare da Fattun dan ta koya mata Yaren sosai,tunda ita ta iya hausa sosai.kuma kusan ahannunta Adeeb ya girma ,ita tayi renonshi. Wai ina batun baffa ne? Allah Sarki baffa lokacin da aka kaishi dakin hukunci ,saida yayi kwana biyu basu wai-waiceshiba,yana can yana fama da zazzabi sakamakon dukan da sukayi masa.sau daya ake kawo masa abinci. Ranar kwana na biyun ne da yamma aka fito dashi dan zartar da hukunci,lokacin mai gari ya danji dama -dama an gyara masa karayar daya samu har uku .jauro kuma yana nan cikin halin bakin ciki,dan kuwa jauronsa ta lalace ,bazata ƙara amfanuwa ba,ta motse ta zama ƴar ririya kamar sillen kara. Shiruwa abokin ta'asar tashi,yanan ido daya ya tsiyaye ,rabin fuska ya zagwanye ,ya zama kamar horo,arɗo ma hannu ya shanye ya zama kamar lauje. Cikin fushi da bacin rai tare da bakin ciki mai gari yace , sakamakon ta'adda cin da baffa da yar shegen daya kawo musu cikin gari sukayi,an karbe duk wasu shanayensa da tumakai harda gidansa ,matsayin diyyar abinda mayyar daya kawo gidansa tayi,sannan ankoreshi daga garin ,saboda ƙarya da cin amanar yan garin da yayi ,na cewa fattu yarsace. Baffa yayi kuka sosai,akan wannan rashin adalcin da akayi masa.amma haka ya haƙura ya miƙawa Allah lamarinsa. Koda ya dawo gida tuni labari ya isa kunne gwogwgo hansai,dan haka yana shigo taci kwalarsa tace ya bata takardar ta bazata iya zama da faƙiri ba. Nan take kuwa baffa yayi mata saki daya .kuma sam ta hana ƴaƴan ta subi baffa. Shi kadai ya bar garin cikin mawuyacin hali. Allah Sarki baffa ,Allah ya saka maka wannan zalumcin da akayi maka. Acan misra kuwa ,amma na hango zaune akan wata ƙayatacciyar kujera , da waya ahanunta ,magana take cike da nuna yanayi na jimami, masu mata hidima na can gefenta azaune. " Zanyi duk iya ƙoƙarin na,ɗan ganin naja yarinyar ajikina, in Sha Allah muke da nasara" amma ta faɗa tana mai ajiye wayar. Murmushi tayi kafin tace" Maryam zaki san koni wacece ,zanyi abinda saiya girgizaki,saina rabaki da dan da kike takama dashi" amma ta faɗa tana mai gutsirar apple. Amma dai itace kishiyar mahaifiyar Adeeb,wacce lokacin da Adeeb yazo ta bar ɗakin mahaifin Adeeb cikin ruɗani. Washe gari da safe fattu ta tashi da wani irin matsanancin ciwon mara,sai kuka take tana riƙe da cikinta. Tsohuwa salima nata rarrashinta tare da bata haƙuri,dan tana tunanin period me zai yiwa fattun. Sosai fattu ke jin mugun ciwon mara,sai murƙususu take cike da azaba tana kiran " Wayyo Hammana zan mutu " Wani irin amai ne ya yunkuro mata,da gudu ta mike ,da nufin zuwa toilet ,saidai taku daya biyu, jiri ya kwasheta ta tafi luuuuuuuu tayi kasa..... Masu karatu masoya,ina godiya da addu'ar ku gareni ,kuma jiki alhamdulillah naji sauƙin sosai , Na gode sosai da kulawa, Much luv sosai da sosai. Mrs babi ce 💘💘💘 Share and comments Fisabilillah. More comments More typing. [7/27, 8:02 AM] +234 703 954 1650: 🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄 MACIJI NE🪱🪱🪱 Na mammy kabeer (Anty mammy) Elegant online writers📚📚 Free book Page 39/40 ________________Wani irin amaine ya tasowa fattu,dan haka da gudu ta mike tana mai riƙe baki,sannan ta nufi toilet.saidai taku ɗaya -biyu tayi kiri ya kwasheta,baya tayi luuuuu!!!zata faɗi.da sauri ta runtse idonta tana mai saki wani ɗan siririn ihu,gaba daya ta gama saddaƙarda cewa ta fadi ,jira kawai take taji ta ina zata fara jin raɗaɗin.saidai maimakon tajita aƙasa,sai taji ta faɗa jikin mutum,wani irin ƙamshine ya ziyarci hancinta mai daɗin gaske,da sauri ta buɗe idanunta dan ganin jikinwa ta faɗa. ido hudu sukayi da Hammanta, dan shigowarsa kenan dakin ya hangota zata faɗi ,shine yayi saurin tarota, dama yana sauka afadar ko gurin mai martaba baijeba yayi sashin ammi,duk kuwa da cewar maimartaban yana ta kiransa awaya akan ya dawo gida . Dan kumshe ido fattu tayi cikin azabar ciwon da mararta keyi ,sannan ta buɗe idonta ,tare da saukesu akan Hammanta,so take ta gasgata shiɗin ne ko gizo idonta keyi. Aikuwa shine wllh Hammanta ne ya dawo,cikin azama kuwa fattu ta rungume Adeeb tare da sakin kuka,dama kuma kukan take. " Hamma ina katafi ka barni?inata nemanka amma banganka ba?dan Allah Hamma karka ƙara tafiya ka barni,kaga bani da lafiya cikinsu ciwo yake min sosai" fattu ta faɗa tana mai cusa kanta aƙirjin Adeeb . Ahankali Adeeb ya lumshe idanunsa tare da rungume fattu shima tsan-tsam ajikinsa,dan kuwa tabbas ba karya yayi kewar fattu sosai ,kullum da ita yake kwana yake tashi,kwana uku da yayi baya ganinta ,jinsa yake kamar mara lafiya. " Is ok stop crying hulwa,ai gani na dawo ko?"ya faɗa yana mai ɗago kanta . Buɗe baki tayi da nufin yin magana ,amma gaba daya aman nan ya taho mata ,aiku ba ɓata lokaci ta wanke Adeeb tass!! Da aman nan ajikinsa. Shikuwa Adeeb ko ajikinsa ,bai damu da aman da tayi masa ba ,ya riƙe ta sosai ajikinsa yana mai shafa bayanta,tausayinta yake ji har cikin ransa,bata da lafiya sosai dole ya kira likita adubata. Tsohuwa salima ce ta karaso garesu tare da faɗin"ayya sannu fateema kinji,maza kawota kaje ka wanke jikinka, wllh tun jiya take fama da ciwon cikin nan,nace yaro kodai girma ne zaizo mata?tsohuwa ta faɗa tana mai kallon Adeeb, Dan sunkuyar da kansa yayi ƙasa yana mai sosa kai,dan ya gani abinda tsohuwa ke nufi,ita haka take dama ba ruwanta idan zata faɗi magana,kai tsaye take faɗi. " Ammm nanny bari na kira likita ya dubata. Ya faɗa yana nufar toilet riƙe da fattu,wanke mata jiki yayi tare da bakinta, shima ya wanke inda ta batashi,sannan ya dawo da ita cikin ɗakin, kwantar da ita yayi akan gado tare da shafa gefen fuskarta yace"sannu yanzu za'a baki magani kinji?"ya faɗa cike da tausayawa,ji yake kamar ya maida ciwon jikinsa. Lumshe ido fattu tayi tare da kamo hannunsa ta rike gam cikin nata tace"Hamma karka tafi dan Allah" fattu ta faɗa tana mai lumshe idanunta . Hannun nata ya riƙe da ɗayan hannunsa kafin yace "ba inda zani zan sake kaya in dawo yanzu" ya faɗa yana mai mikewa tare da ficewa daga dakin. Tare suka dawo shida likita,wadda ta kasance likitar gidan ce , mai duba mata. Sosai ta duba fattu ,kuma ta gane period ke don zuwa mata ,kuma farkon yine shiyasa take jin ciwo. Dan haka bayani tayiwa Adeeb tare da bashi magungunan da Fattun zata sha.sannan ta lika always Jikin pant taba nanny akan idan jinin yazo saita bata tasanya. " Yawwa Ni dama nayi tunanin ko girma ne zatayi ,dan ciwon yayi yawa,Allah Sarki ashe kuwa shine ,bari na haɗa mata tea mai zafi ta sha"nanny ta faɗa cikin tausayawa tana mai nufar kitchen. Shidai Adeeb yana zaune bakin gado,tunda yaji abinda ke damun fattu,baice komai ba ,kawai yana kallonta dan ta ɗan sami barci . Cikin girmamawa likitar tayiwa Adeeb sallama ta fita akan zata dawo anjima . Kai kawai ya ɗaga mata ba tare da ya kalletaba. Kusan minti biyar saiga nanny ta dawo riƙe da wani kyakykyawan kofi sai turiri yake ,mikawa Adeeb kofin tayi tana mai cewa" ungo magajin faɗa tashe ta maza ta sha zatayi daɗi,kuma jinin zai sauko da wuri" ta faɗa tana mai nufar ƙofa again tana cewa " bari i ke in kula da farfesun can dana ɗora mata,kasan shima yana taimakawa mace idan tana jini"ta faɗa tana ficewa. Kallo Adeeb ya bita dashi,yana mai girgiza kai,yana son tsohuwar nan ,saidai tacika surutu da sanya mutum jin kunya. Ahankali ya ɗan shafe fuskar fattu da tayi wani fayau da ita ,sai kyalli take,ahankali ta buɗe idanunta tare da saukewa akan kyakykyawar fuskar hammata. "Hamma" ta furta ahankali tana kallonsa. " Tashi Kisha tea maza" ya faɗa yana mai taimaka mata ta zauna bayan ta sanya mata fillo abayanta. Da kansa yake bata tea ɗin abaki,saida tasha kusan rabi sannan tace ya isheta, ajiye sauran yayi yana mai kallonta kafin yace" ya kike jin jikin naki?" " Da sauki Hamma saidai jikina ba kwari ,kuma har yanzu inajin ciwo anan dina"fattu ta faɗa tana mai nuna masa saitin marar ta. Kawar da kai yayi da sauri yana mai cewa" is ok zai daina " " Hamma zanyi fitsari" fattu ta faɗa ahankali. Dan kallonta yayi kafin yace " zaki iya zuwa toilet ɗin?" Kai ta daga masa tana mai yunkurawa ,tashi tayi tsaye tana ɗan yamutse fuska. Sai taji kamar lema ajikinta,juyawa tayi tare da kallon inda ta tashi,zato idanu tayi lokacin data jini agurin,da sauri ta kai hannunta ta shafo bayanta ,tana mai kallon hannun,aikuwa jini ne kuma daga jikinta ya fito,ƙara zato idanu tayi cikin tsoro tana mai faɗin" na shiga ukuna Hamma jini ,jine yana zuba ajikina,wayyo Allah Hamma jini"fattu ta faɗa tana mai nuna masa hannunta ,jikinta na rawa sosai kamar ana kada mata gangi, Kallonta Adeeb yayi da sauri ,yana mai kallon hannun nata ,lumshe idanu tayi yana mai jin wani iri ajikinsa,tausayi fattu ke bashi,ita bata san komai ba ,yanzu meye abin damuwa akan wannan ga yadda jikinta ke rawa kamar ana yankata.? Ahankali ya mike tsaye tare da dafa kafadun fattun yace " ki nutsu mana ,wannan ba wani abun damuwa bane kinji dama hakan na faruwa ga ko wace mace data kai shekaru irin naki" yayi shiru yana ɗan sauke nunfashi ahankali. Fattu kuwa kuka take tana cikin tashin hankali,sam Bama tajin me Adeeb ke faɗi,sai cewa take " Hamma jini ajikina, dan Allah kace ya daina zuba ,na shiga uku jinina zai kare wayyo baffana" abinda take fadi kenan jikinta na rawa . Gaba daya Adeeb yana rasa me zaicewa fattu,dan haka kallonta kawai yake cikin damuwa,suna cikin haka saiga nanny ta shigo, ajiyar zuciya Adeeb yayi tare da kallon nanny amarairaice. " Aa meke faruwa ne haka magajin faɗa?(da yake haka take kiransa) taci gaba ,naga fateema na kuka ,kaikuma ka tasata gaba da kallo kaima kamar salati kukan?nanny ta fada tana mai karasowa cikin dakin. Ahankali Adeeb yace "nanny kiyi mata bayani kuka take, wai bata so" ya faɗa kamar zaiyi kuka. "Yau naga ikon Allah fateema meye baki so?ko maganin ne baki don sha?kiyi haƙuri ai lafiya ake nema miki kinji ?kuma da kinsha jinin zai....sai kuma tayi shiru tare da bin gadon da fattu ta tashi da kallo,to kace jinin ne yazo ,wato shi tagani take cewa bata so,Allah Sarki ai zaki saba dayake wannan ɗin na farko ne ,zo muje In gyara miki jiki yi shiru" nanny ta faɗa tana mai kamo hannun fattun suka nufi toilet. Kallonsu Adeeb yayi tare da sauke ajiyar zuciya ,sannan ya fice daga ɗakin,bayan ya janye zanin gadon daga kan gadon,ya ajiye gefe guda,tare da shimfida wani. Kai tsaye gurin mai martaba ya nufa,yana shiga ya tadda mai martaba tare da amma, zama yayi kusa da mahaifin nashi,bayan ya jefa wa amma wani kallon na tsana . Kawar da kai amma tayi tare da sakin murmushin gefen baki tace yaro yarone ,cikin zuciyarta. " Habeebee Barka da dawo ,yanzu nake ƙoƙarin sake kiranka,ai najika shiru,kasan yanzu bana son koda da minti ɗaya ka ƙara nisa dani"abie ya faɗa yana mai shafa kan Adeeb. Murmushi Adeeb yayi tare da sumbatar hannun mahaifinsa kafin yace " abie wancan karon ma ,kaddarace ta sameni,har Allah ya ba maƙiya nasara akaina,saidai ahalin yanzu kar nake kallon,kowa sannan ba abinda mutum ya isa yayimin na cutarwa in Sha Allah" Adeeb ya faɗa yana mai kallon ammi cike da tsana . Itama ammi kallon Adeeb take ,tana mai suna maganganunsa ,kafin ta sauke ajiyar zuciya tayi sallama da mai martaba tare da ficewa daga ɗakin. Waya ta dauko tana mai kiran wata number tace " mu hadu yanzu-yanzun nan" sannan ta kashe wayar. Adeeb yana fitowa daga ɗakin abie ya nufi bangaren da amminsa ke hutawa, Wayace akunnenta kuma da alama wayar da take mai muhimmanci ce ,saidai tana hango Adeeb ya tunkarota tayi saurin katse wayar tana mai cewa " zan kira -zan kira" bata jira amsar dayan vangaren ba ta kashe wayar. Zama yayi kusa da ita tare da kamo hannunta ya sumbata, kanshi ta shafa taba faɗin Allah yayi maka albarka. Ya jima suna dan hira ,kuma duk akan kunyar fattun ne ,kafin ya mike yace zaije ya huta. Ƙura mata ido naga ammi tayi ta baya ,kuma fuskarta amugun hade ,kafin kuma tayi wani murmushi tana mai jinjina kanta.... Masu karatu manage , Yau naje gidan suna ne. Saida na dawo nayi wanna typing ɗin. Much luv. Mrs babi ce💘💘 Share and comment fisabilillah. [7/27, 8:20 PM] +234 810 779 7743: 🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄 MACIJI NE🪱🪱🪱 Na mammy kabeer (Anty mammy) Elegant online writers📚📚 https://facebook.com/groups/943534712916776/ Masu amfani da Facebook sai kuyi join wan nan link din👆🏽 Free book Page 41/42 _______________Adeeb yana barin gurin saiga rashy ya ƙaraso,zama yayi kusa da mahaifiyar tasa tare da sumbatar hannunta, Kansa ta shafa tana faɗin ",magajin faɗa prince Rashad Muhammad ashraf"ta faɗa cike da jin dadin sunan. Turo baki Rashad yayi tare da kallon ammi yace " ammi ta yaya zan zamo magajin fadar?bayan kinƙi yin wani abu akan wannan al'amari,ki dubafa,Adeeb ya dawo gida,kuma cikin ƙoshin lafiya yake,kina tunanin abie zai bar Adeeb ne,sannan Ni ya ɗorani akan karagar? Shiru ammi tayi tana kallon Rashad har ya kai ƙarshe azancensa,kafin tayi wani murmushi kana tace " Rashad kenan,kasan dai Adeeb yana jin maganata,sannan baya tsallake umarnina, yanzu akwai Abinda nake tunani akan yarinyar can ,daya zo da ita. Ina son tabbatar da wani abu ne game yarinyar ,wannan sarƙa ta wuyanta tabbas nasan iyalan dake da irin sarƙa,kuma sun rasa yarinyar su tsawon shekaru, Amma idan har na tabbatar da zargina akanta,to zanyi iyakar ƙoƙarina na ganin bata haɗu da ahalin nata ba,dan haduwarsu da ahalin babban koma bayane agareni. Masanin ido kawai ,zakaga abinda zanyi akan wannan al'amarin. Murmushi Rashad yayi tare da jin wani sanyi cikin ransa,dan yasan tabbas mahaifiyar tasu zatayi ƙoƙarin akan wannan al'amarin. "Amma ammi Zulaihat fa?kinsan yadda take ƙaunar Adeeb ,kada ta bamu matsala"cewar Rashad kenan yana gutsirar dabino . "Barni da zulaihat,bana jinta ko kaɗan ,yarinyar da ba wani hankali ta cika ba,itama bazan bari ta auri Adeeb ɗin ba ,lokaci kawai nake jira in maidata can gida"ammi ta faɗa cike da murmushi akan fuskarta. Sun jima suna tattauna ita da Rashad agurin ,kafin suka koma cikin gida. Fattu kuwa suna shiga toilet nanny ta hada mata ruwan wanka mai zafi,tace tayi wanka maza. Bayan tayi wankan ne ,nanny ta bata wannan pant din tasa ajikinta ,sannan suka fito,har zuwa lokacin kuka fattu keyi,har yanzu jinin bai daina zubowa ba,yanzu idan jinta ya kare ya zatayi?mutuwa fa zatayi kenan. Nanny sai rarrashinta take akan taci farfesun nan tasaha magani amma taki,kuma har lokacin marar ta ciwo take mata. Suna cikin haka saiga Adeeb ya shigo ɗakin,tana ganinsa jikinta ya ƙaru.tun kafin ya zauna ta fara magana. " Hamma na shiga uku har yanzu jini na zuba yake ,tsoro nake karya kare In mutu,dan Allah Hamma ka taimaka min" fattu ta faɗa tana mai miƙa masa hannu cikin kuka sosai. Da ɗan sauri Adeeb ya ƙaraso kusa da ita ya zauna,kallonta yake cike da tausayi,kafin ya riƙe hannunta wanda take miƙa masa yana ɗan murzawa kana yace" kina so ya daina zubowa " ya faɗa cikin sanyin muryarsa. Da sauri fattu ta jinjina kai tana hawaye. " To kiyi shiru,ki daina kuka, sannan ki nutsu kici abinci Kisha magani,zakiga ya daina zubowa" Adeeb ya faɗa yana mai share mata hawaye wasu na zubowa. "Hamma da gaske idan na daina kukan zai daina zubowa Ni tsoro nakeji kar jinina ya ƙare" ta faɗa cikin muryar kuka tana mai shagwabe fuska. Jinjina mata kai yayi yace " sosai ma kuwa,kuma jininki bazai ƙare a idan kika daina kuka" Ahankali fattu ta sanya bayan hannunta ta share hawayen,tana mai kallon Hammana nata. Farfesun ya karba ahannun nanny ya fara ɗiba da cokali yana bata abakin,haka take cin farfesun kamar magani,kusan lokaci shida tayi tace ta koshi. Bai takura mata ba,ya ajiye flate ɗin ,magungunan ya bare tare da miƙa mata.yamutse fuska tayi tana mai turo baki,alamun bata so. Kallonta Adeeb yayi kafin yace " ok baki son abun ya tsaya kenan?" " Ina so Hamma amma Ni bana son wannan abun aradu" ta fada cike da shagwaba, kafeta yayi da idanunsa masu matuƙar haske da ɗaukar hankali,wani irin yakeji idan tana masa shagwabar nan,nan take zaiji jikinsa yayi week, kasala ta lullubeshi ,gara yayi ya bata maganin nan kar ayi abin kunya gaban nanny. Hannunsa yaji fattu ta kama cikin nata tattausan hannu ,wani yuummmmm!! Yaji gaba ɗaya jikinsa ya ɗauka ,ahankali ya lumshe idanunsa yana mai sauke ajiyar zuciya. " Hamma zansha to kabani"fattu ta faɗa tana mai ƙara damke hannun Adeeb cikin nata. Ƙara damke idanunsa yayi tamau yana mai fidda wani sauti da ɗan sauri,kusan minti biyu idanunsa na runtse ,kafin ya budesu,har sun sauya kala daga fari tas zuwa ɗan jaa kadan. Ahankali ya zare hannunsa daga cikin nata,jikinsa sam ba kwari,maganin ya mika mata ,buɗe baki tayi ya saka mata maganin sannan ya bata ruwa.da gyar ta hadiye maganin tana ƙoƙarin yin amai. Janyota yayi zuwa jikinsa ya rungume ta tsam-tsam ,yana ɗan shafa bayanta slowly. Lumshe idanu fattu tayi tana mai shaƙar daddaɗan kamshi jikin Adeeb,lokaci guda kuma taji ciwon marar ta na raguwa sosai. Shima Adeeb idanu arufe yake shafa bayan fattu,yana mai jin wani yanayi atattare dashi ,dadinsa ma nanny ta bar ɗakin tuni.dan haka gyara zama yayi ,tare da jingina bayansa jikin gado.sosai yake jin dadin yanayin da suke ciki ahalin yanzu,gaba daya yanayinsa ya sauya.sosai yake jin kansa cikin hali na buƙatuwa,wanda har wani hucin iska yake fesarwa daga bakinsa. Ahankali ya dago kan fattu tare da ƙura mata idanu,itama kallonsa take ,dan wani iri takeji ajikinta,bata san me takeji ba,amma kawai tana so hammanta yayi ta shafa mata bayanta. Ahankali Adeeb ya kira sunanta" Hulwa"can cikin makoshinsa,kallonsa take jin ya kira sunan Hulwa kuma yana kallonta. Bai damu da kallon da take masa ba yaci gaba da magana " me kike buƙata yanzu?ina ne yake miki ciwo" ya faɗa kamar mai yi mata rada asaitin kunnen ta. Da sauri ta ƙanƙame dantsen hannusa tana mai lumshe idanunta,dan wani irin abu dataji yana mata yawo cikin jikinta,lokacin da sautin muryarsa tare da iskar bakinsa suka doki kunne ta. "Hammmma" ta furta ahankali cikin jan sunan. Kallonta yake tare da karantar yanayin da take ciki,ko shakka babu yasan tana jin makamancin abinda yake ji ajikinsa,saidai shikam baida niyyar cutar da fattu,ko kaɗan dole yake nesanta kanshi daga gareta ,dan gudun faruwar wani abu. Ahankali ya ƙara maimaita mata tambayar ,saidai wannan karon bai kai bakinsa saitin kunnenta ba. "Hannunsa fattu ta kamo tare da ɗorawa asaitin mararta" marar Tata kuwa tayi zafi sosai ,kallon fuskarta Adeeb yayi wacce har yanzu idanunta ke rufe, "Nan ke miki ciwo" Adeeb ya faɗa ahankali muryarsa na dan rawa. Jinjina kai fattu tayi ba tare da ta buɗe idanunta ba. Ahankali ya kwantar da ita akan gadon,sannan ya ɗan daga doguwar rigar dake jikinta,nan take santala -santalan farare cinyoyinta suka bayyana,kallo Adeeb yabo cinyar Tata dashi,yana mai ambaton sunan Allah cikin ransa. Ahankali yake ɗan shafa marar Tata tare da dan dannawa kadan kadan ,kamar yana mata tausa , shiru fattu tayi tana jin wani irin sanyi da daɗi na ratsa dukkan sassan jikinta,sosai take jin dadin abinda Hamma ka mata,dan kuwa tuni ta nemi ciwon mararta ta rasa,sai wani nishi take ahankali tana mai riƙe zanin gadon .kwantowa Adeeb yayi tare da ƙurawa lips ɗin ta idanu,buɗe ido fattu tayi tana mai kallon fuskarsa, Kusan minti biyu suna kallon juna,kafin Adeeb yaji bazai iya ɗaurewa ba kawai ya hada bakinsu guri ɗaya ya fara kissing ɗin fattu. Kusan mintina biyar zuwa bakwai suka ɗauka cikin wannan halin,gaba daya Adeeb ya fice daga hayyacinsa ,Banda nishinsa ba abinda kake juyowa aɗakin,yayinda fattu kuwa tayi lakwas tana amsar sakonsa, da alama dai itama tana karbar sakon yadda ya kamata. Kamar wanda aka tsikara,Adeeb yayi saurin zare bakinsa tare da mikewa yayi hanyar fita daga dakin yana tangadi kamar ɗan giya. Fattu ma saurin juya bayanta tayi tare da runtse idanunta,wani irin abu takeji yana yawo ajikinta ,kuma bataso hamma ya daina mata wannan abun ba sam. Adeeb yana fitowa daga dakin fattu sukayi kiciɓis da Rashad shikuma yana shigowa babban falon, Baki sake tashar ke kallon Adeeb ,ganin yanayin da yake ciki,kar dai ace Adeeb zagayawa yake gurin yarinyar nan fa? Dan kallo daya Zakayiwa Adeeb kasan yana cikin hali na buƙatuwa. Kodai dama kafuwarta ce bamu sani ba ?yace taimakonsa tayi shima yake son taimakonta?(Dan ba Wanda yasan meye alaƙar dake tsakanin fattu da Adeeb ,hatta mai martaba ,sam Adeeb bai fada masa ba. Shikuwa Adeeb ko kallon inda Rashad take baiyiba ,yayi ficewarsa daga ɗakin,Dan shikadai yasan meke damunsa. Kai tsaye Rashad ya nufi dakin da fattu ke ciki,tana kwance har lokacin bata ko motsaba, kallonta yake cike da tsantsar sha'awar ta ,abun tayi ta ko ina kalli hips ɗin ta kamar zai fasa rigar nan,ahankali ya Rashad ya ƙarasa bakin gadon yana mai karewa fattu kallo ,wani irin kashe ido yake yana mai jin kamar ya ruƙunkumeta ajikinsa,hmmmmm Allah ya kamu gobe ,ko kaɗan bazan saurarawa babyn nan ba,Rashad ya faɗa yana mai miƙa hannu da nufin taba abinda ke taimake masa idanu ajikinta. " Kai- kai ɗan nan menene haka?me zakayi mata ajikin nata ?zo maza ka fice" nanny ta faɗa tana nuna masa hanyar waje. Dan sosa kai Rashad yayi yana mai hararar nanny kafin ya fice daga dakin yana faɗin "wllh tsohuwar nan ta fiye samun guri,duk wannan banzan ne ya bata dama ,amma zanyi maganinta ne.ya faɗa yana mai ficewa daga ɗakin. Ammi kuwa waya ta dauka tare da kiran wata number,bugu biyu aka daga ,murmushi ammi tayi tana faɗin " ƙawatafatan dai kina hanya ,zakizo gurin taron namu ?" Ta can daya bangaren bansan me akacewa ammi ba ,na dai ji tace "hmmmmm ke dai ki bari kawai saikinzo dan akwai gagarumar matsala sosai" Shiru ta ɗanyi kaɗan kafin tace " shikenan Allah ya kawoki lafiya dole mu san abinyi" ta faɗa cike da daure fuska. Ajiye wayar tayi tare da yin shiru ,da'alama tayi zurfi cikin tunanin mafita. Adeeb kuwa yana shiga part dinsa ya zube akan kujera,ko takalmin bai iya cire wa ba ,kwanciya yayi rub da ciki akan kujerar ,idanunsa alumshe ya dafe mararsa da hannun damarsa ,fuskarsa ayamutse. Sai huci yake sauƙewa. Wayarsa ce take ta faman ringing ,Amma ya kasa ɗagawa,haka tayi ta ƙara harta tsinke. Dole ya ɗauki mataki ,dan gaskiya yana cikin matsala ,idan haka taci gaba da kasancewa to zai shiga damuwa matuka. Ajiyar zuciya sauke arako na ba adadi,yana mai kara damke mararsa,ba abinda yake ji dagani sai fattu kwance kan ƙirjinsa,yayinda yanayinsa ke kara yin nisa. "Washhhh " ya furta ahankali yana mai dantse lips ɗinsa na ƙasa. Nan da nan jikinsa ya kama rawa zazzaɓi mai zafi ya rufeshi ruff.. Muje zuwa masu karatu. Anty mammy ce Mrs babi💘💘 Share and comment Fisabilillah. [7/29, 9:05 AM] +234 810 779 7743: 🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄 MACIJI NE🪱🪱🪱 Na mammy kabeer (Anty mammy) Elegant online writers📚📚 Free book Page 43/44 _______________"Washhhhhh "Adeeb ya furta ahankali yana mai dantse lips ɗinsa na ƙasa, cikin azaba da radaɗin ciwo,juyi kawai yake akan kujerar,banda bari ba abinda jikinsa keyi,ko yaya ya runtse idanunsa Hulwa yake hangowa,gaba daya ya kasa cire moment ɗinsu,na dazu cikin zuciyarsa,kuma duk lokacin daya hasko moment ɗin ,ji yake tamkar anƙara masa zafin ciwon ne. Nan da nan cikin lokaci ƙanƙani zazzaɓi mai zafin gaske ya lulluɓeshi.duƙunƙunewa yayi akan kujerar yana mai rawar ɗari da fidda wani irin nishi na azaba. Wayarsa ce ta ɗauki ƙara akaro na biyu,amma ko inda take bai kallaba hatta tsinke. Shikuwa tareeƙ da yaji wayar nata shiga kuma ba'a ɗagaba,sai kawai ya shigo part ɗin Adeeb ɗin ta baya.dama shike kiransa tun dazu ,yana don zasu tattauna akan wata magana. Shigowa yayi cikin falon da sallamarsa,bayan yayi ta nokking yaji shiru. Kallo yabo falon dashi aƙoƙarinsa na gano inda Adeeb ɗin yake ,dan yafi tunanin ma yana ɗaki. Saidai kuma akan kujera ya hango Adeeb ɗin cikin mawuyacin hali,da sauri ya ƙarasa gareshi yana mai durƙusa akasan kurar da Adeeb ke kwance.cikin rikicewa yake faɗin" yallaɓai lafiya kuwa?meke faruwa?baka da lafiya ne?tareeƙ ya faɗa cikin ruɗu yana mai taɓa jikin Adeeb ɗin.aikuwa jikinsa yayi zafi ƙau kamar wuta. Ahankali Adeeb ya buɗe idanunsa tare da ɗan juyowa ,dan da ya tura kansa ne jikin kurar ya bada baya.kallon tareeƙ yayi cikin mayen ciwo kafin yace " tareeƙ bani magani Please my seek" ya faɗa yana mai jihar da kansa yaci gaba da kwanciya. Da sauri tareeƙ ya mike tare da shiga uwar ɗakan Adeeb dan dauko maganin. Wow masu karatu wato yadda Adeeb yake na daban ,haka komai nashi yake na daban,Dan karkuso kufa haduwa adakin Adeeb,komai na cikin uwar dakan,pich ne da milk ,hatta silafas ɗin toilet pich ne jikinsa da milk.banda ƙamari ba abinda dakin keyi. Maganin tareeƙ ya dauko,dan yasan meke damun yallaɓai ɗin nasa,lokaci zuwa lokaci yakanyi wannan irin ciwon marar. Ruwa ya dauko cikin fridge ,sannna ya ƙaraso kusa da Adeeb ,maganin ya ɓallo tare da miƙa wa Adeeb ɗin yana mai cewa" yallaɓai ga maganin" Saida Adeeb yayi kusan minti biyu kafin ya yi ƙura da gyar ya tashi zaune hannunsa riƙe da mararsa, wacce take mugun mirɗa masa,har wani ƙara take. Karɓar yayi tare da kaiwa bakinsa ,sannan ya kora da ruwa yana sauke numfashi da sauri da sauri.idanunsa sunyi mugun jama'a,sun ƙanƙance.ahankali ya furta " na gode tareeƙ" ya faɗa idanunsa alumshe ya jingina da jikin kujerar. " Yallaɓi aikinna ne kula da lafiyarka, dan bani da wani ɗan uwa daya wuceka, daga mahaifiyata saikai nake kallo inji daɗi,amma yallaɓai inaga lokaci yayi da yakamata akawo karshen wannan ciwon,abin yana matukar damuna"tareeƙ ya faɗa kamar zaiyi kuka,dan harga Allah baya ƙaunar ganin Adeeb cikin damuwa ko ƙanƙani. Adeeb ya ɗauke tamkar ƙaninsa da suke ciki ɗaya,tun suna yara suka taso tare,dan tareeƙ ɗan gidan nanny ne,mahaifinsa ya rasu tun yana yaro,agidansu Adeeb ya rayu da mahaifiyarsa,cikin kulawa da nuna kauna . Ajiyar zuciya mai ƙarfi Adeeb ya sauke dan marar tasa ta fara lafawa,kafin yace " karka damu tareeƙ komai zaizo karshe in sha Allah " ya faɗa yana mai kwanciya akan kujerar. Jinjina kai tareeƙ yayi tare da kallon Adeeb cikin tausaya wa yace " yallaɓai ko zakayi wanka? Jinjina akai kawai Adeeb yayi alamun ehh zaiyi" tareeƙ da kansa ya haɗawa Adeeb ruwan wanka kafin yazo ya sanar da shi. Mikewa Adeeb yayi lokacin jikinsa ya haɗa zufa sosai ,kan tareeƙ ya shafa cikin murmushin ƙarfin hali kafin ya shige cikin dakin. Binsa da kallo tareeƙ yayi cike da mugun ƙaunarsa aransa, akwai abubuwa da yawa da yake son sanar da uban gidan nasa,saidai yana tsoron ta yadda zai karɓi maganar ,dan kuwa hankali bazai taba daukar abinda yake son sanar dashi ba,amma zaiyi iyakar ƙokarinsa wajen bawa Adeeb kariya ga duk masu don kawo masa hari arayuwarsa. Amma ce zaune cikin ɗakinta,yayin da Rashad ke zaune shima kusa da ita ,fuskarsa sam ba walwala, da alama dai suna tattauna wata magana ne mai muhimmanci, "Rashad bana son irin rayuwar da kakeyi ko kaɗan,sam baka jin maganata,ka maida ammi itace uwarka itace ta isa dakai,kasani ba'a yarda da kishiyar uwa dan wasu ba alkairine azuciyarsu ba,Ni dai nina haifeka ,kuma kasan bazan taɓa cutar da kaiba,amma ka haɗa kai da maƙiyiyata sai abinda tace kakeyi ,to wllh ka kiyayeni,idan na juyo kanka bazakaji daɗi ba,yau kusan kwana uku baka ko leƙo dakin nan ba da sunan ka ganni ,sai yau da kazo min da wani zancen banza,to ina mai gargaɗinka akan yarinyar nan ba ruwanka da ita,kasan halin Adeeb sarai ,kome yayi maka kaika sani" amma ta kai ƙarshen batunta tana mai huci da jin ciwo cikin zuciyarta,sam Rashad bai ɗauke ta matsayin uwa ba,ya mika al'amarinsa kaf ga ammi ,hakan na matukar yiwa amma ciwo,yazo su hada kai susan me suke ciki amma yaƙi. Rashad kuwa banda hura hanci ba abinda yake,yana zatace wani wai baruwansa da babyn na?wannan ma ai shirmene,wllh saidai kome zai faru ya faru ,amma ya gani ya gyasa kuma saiya ɗana.ya faɗa cikin zuciyarsa,kafin ya mike cikin rashin biyayya ga mahaifiyar tasa yake magana" nufa ba wanda ya isa ya hanani yin abinda naga dama,ke dayake hanaki naki uzurin, ko kina tunanin duk irin mugun abinda kike ƙullawa Adeeb ɗin ban sani ba?wllh idan aka takuramin zan fasa kwai ba ruwana,kinji kinsawa mata ido,baiwar Allah ita kuma tana ta nunawa danki so da kulawa" Rashad ya faɗa cikin rashin kunya yana ficewa daga ɗakin. Kallonsa kawai amma keyi,idan da sabo yaci ace ta saba da rashin kunyar rashad,sam baya ganin girmanta, amma zatayi maganinsa. Ta faɗa cikin ranta tana mai tunanin yadda zata wulaƙanta ammi cikin ruwan sanyi. Fattu kuwa barcine yayi nasarar ɗauke ta ,har cikin barcinta mafarkin Hammana tayi tayi,yana mata wasanninsa masu nutsar da jiki da zuciya .sai kusan la'asar kafin ta farka daga barci,ba laifi marar ta daina ciwo,dan likatar nan ta dawo dan ta dubata lokacin tana barci . Wanka nanny ta sata tayi tare da bata wata always ɗin ta saka bayan ta lika mata jikin pant.abinci taci tasha magani sannan ta zauna akan gado tana kallon Film ɗin da nanny ta kunna mata jikin kayan kallo. Ta maida hankalinta sosai tana kallon Film ɗin ,indian yayinda take ganin kamar itace da Hammana suke lobayya.lol Nanny ce ta shigo ɗakin ta zauna kusa da fattu tana mai faɗin" sannu ƴar nan ya jikin naki? Nanny ta faɗa tana ajiye wani bolw duke da kayan marmari a cikinsa. Kallonta fattu tayi tare da sakin murmushi,dan tana ƙaunar matar har cikin zuciyarta,tana da kirki ga kulawa da mutum,dan zaman da sukayi sosai fattu ke cintar wasu kalmomin na larabci,saidai baya iya maidawa ba. Jinjina kai tayi alamun da sauƙi, kafin ta fara cin apple.sosai take jin dadin wannan abun mai kama da dankali aradu idan tanacinsa har wani lumshe ido take. Ammi ce ta shigo ɗakin cikin shigar ta ta koda yaushe wato doguwar riga mai shegen kyau da ɗaukar ido,gaba daya jikinsa sarkokin gwal ne ,sai ƙamshi take bugawa,cikin murmushi take shafa fuskar fattu tare da mata ya jiki,sunkuyar da kai fattu tayi cikin kunya,bata e komai ba. Kallon wuyan fattu ammi tayi, tare da kafe sarƙar wuyan nata da ido,tabbas tasan wannan sarƙar da masu alaƙa da ita,amma ta yaya sarƙar zata kasance a wuyan wannan yarinyar,lallai dole ta raba ta da sarƙar nan dan kawar da zargi.zama tayi abakin gadon,cikin murmushi tana shafa lalausan bakin gashin fattu,kafin ta kalli nanny cikin murmushi tace " nanny ƴar taki fa akwai kunya sosai,ban sani ba kodai sirikata ce ita?da alama ko suna soyayya da dana ne " ta faɗa tana mai shafa sarƙar da hannunta. Murmushi nanny tayi wacce ke tsaye can gefe tun shigowar ammi dakin,kafin tace " ranki ya dade gimbiyar uwar magajin faɗa,ba wannan alamun atare dasu,yana mata kallon ƙanwa itama tana masa kallon yaya ne,wannan shine abinda na fuskanta atsakaninsu" nanny ta faɗa cikin murmushi tana kallon fattu. Murmushi itama ammin tayi,tana mai jin wani sanyi cikin ranta,yanzu ta sami nutsuwa ,akan ba wata alaƙa atsakaninsu,saura biye duk wata alama da zata sa agane iyayen fattu. " Nanny kawo mata lemo mana ,naga ba wani drinks agabanta " ammi ta faɗa dan son fitar da nanny ɗaga ɗakin. Da sauri nanny ta fice tana faɗin " angama ranki ya dade" tana fita ammi ta kalli fattu tare da sakar mata wata uwar harara,ta gefe ,kafin ahankali cikin dabara ,ta yadda fattu bazata taɓa tsammanin ancire sarƙar wuyanta ba ,ammi ta zare sarƙar tare da damkewa cikin hannunta. Lokacin da take zare sarƙar ,da sauri fattu ta kai hannunta dan jin abu yana ɗan yawo awuyanta. Cikin sauri ammi tace " ayya ƴata bari incire miki wani ɗan zarene awuyan naki" ta faɗa tana mai karasa cire sarƙar. Nanny na shigowa ita kuma ammi ta mike tare da ficewa daga ɗakin cikin tsantsar farin ciki.da alama komai zaizo mata cikin sauƙi. Adeeb kuwa bayan yayi wanka ya huta,sannan yaci abinci kaɗan ,kafin ya janyo computer yana ɗan wasu ayyukan da ita,har lokacin yana jin ciwon marar kaɗan,saidai ba zazzaɓin.yana aikin ne kawai amma zuciya da tunaninsa suna kan fattu,dan so yake yaga Wane hali take ciki.kasa ɗaurewa tayi ya dauko wayarsa ya kira nanny, Tana dagawa ta ce " magajin fada ɗana ɗan albarka,me kake buƙata. Murmushi yayi yana mai ɗan kumshe idanunsa,bayan amminsa nanny itace uwar riƙonsa da bazai taba daina ƙaunarta ba.cikin sanyin murya irin ta masu jinya yace "nanny ya jikin nata" ? "Jiki kam da sauƙi ka gantama tana kallo bari na bata wayar." Cewar nanny Tana mai karawa fattu wayar akunne. "Hmmmmm Indai wanna ce Allah yasa tasan me ake yi da wayar ma"Adeeb ya faɗa cikin zuciyarsa. Fattu kuwa kallon nanny tayi jin ta ƙara mata waya akunne,meye kuma wannan haka ?nanny ta doramin akunne na? Fahimtar kamar fattu bata gane me zatayi da wayar bane yasa nanny tace " yayanki ne Adeeb ya ke magana,riƙe bari naje kitchen" nanny ta faɗa tana damkewa fattu wayar ahannunta. Kallon haɗaɗdiyar wayar fattu tayi tana mai cewa acikin" Hamma kuma anan,to ta yaya yashiga cikin wannan ɗan karamin abun har yake magana?wayyo Allah na ta yaya Hamma zai fito ?na shiga ukuna Hamma kana ina ?kana jina ?dan Allah ka fito" fattu ta faɗa cikin muryar kuka,nan da nan hawaye ya fara wanke mata fuska. Lumshe idanu Adeeb yayi ta can bangaren dan yana jin duk abinda yake fadi,kuma yasan za'ayi hakan .ya rasa wane irin shirme ke samun fattu,yanzu inda zuwa yayi ta ganshiba shikenan zatayi ta kukane gashi bata da lafiya. Mikewa yayi da sauri ya nufi ƙofa. Rashad ne tare da ammi suna tsaye jikin wata ƴar ƙaramar runfa mai kama da bukka ,magana suke mai muhimmanci,dan kuwa sai murmushi Rashad keyi yana kallon ammi. " Aikuwa ammi yanzu zanje na ɗan ganta dan wllh ko barci bana iyayi,gaba daya babyn ta rikitani " rashad ya faɗa yana mai dage gira daya. Dariya ammi tayi kafin tace " maza ɗan jeka abinka ,ba mai hanaka abinda ranka ke so,amma karka sake kayi mata komai,kajira lokaci,kawai kaje ka ganta kasami nutsuwa ranka" ta faɗa tana mai shafa kan Rashad din. Murmushin jin dadi yayi tare da sumbatar hannun ammi,yace " shiyasa nake sonki fiye da mahaifiyata ammina"ya faɗa yana barin gurin. Wani shegen murmushi ammi tayi tana mai binsa da kallo kafin tace " dani kike magana hafsat, nayi alƙawarin saina kawo karshenki afadar nan, keda ɗanki.koba dani zakiyi gasa ba?muje zuwa" ammi ta faɗa cike da gadara tana kaɗan kai. rashad na shiga dakin da fattu take ya ganta zaune tana kuka,ga apple ɗin ta ahannu wani abaki,cike da shaukin babyn ya ƙarasa inda take ya zauna kusa da ita sosai ,da sauri fattu ta matsa can gefen gadon tana kukanta. "Ohhh baby menene kike kuka?masu kyau ga basa kuka kiyi shiru,fadamin abinda ke saki kuka ?ko zakuɗa chocolate?ko ice cream kike so,Rashad ya faɗa yana mai ƙara matsawa kusa da fattu sosai . Yunƙurin mikewa fattu tayi daga gurin da take ,dan ya kunaceta sosai,rashad yayi saurin janyota jikinsa ya rungume ta, ta gefe" haba babu kiyi shiru mana bana son ganin ki cikin damuwa,zo in baki chocolate kinji" ya faɗa yana ƙoƙarin hade bakinsu guri daya bayan ya riƙe fuskarta. Cikin kuka fattu ta hankaɗe shi tare da fitowa daga kan gadon tayi kofa da gudu tana kuka.biyota yayi shima,saidai kafin ya ƙaraso ta buɗe kofar ,tana buɗewa kuwa taji ta faɗa jikin mutum,da sauri cikin tsoron ko rashad ne fattu ta dago kanta tana kallonsa. Ai tana ganin Adeeb ne tayi sauri ƙanƙameshi tana kuka. Riketa yayi da sauri shima yana mai shafa bayanta ahankali,idanunsa alumshe" ya isa haka ba gani ba ?ki daina kukan " Adeeb ya faɗa yana mai dago kanta. Cikin kuka fattu take nuna masa rashad" Hamma kace ya fita bana son ganinsa tsoro yake bani"ta faɗa tana mai ƙara kwantar da kanta aƙirjin Adeeb. Da sauri Adeeb ya dawo kansa ,aikuwa carab idanunsa ya sauka akan na rashad,wanda yayi tsilli -tsilli dashi yana kallonsa. Cikin wata irin zuciya da ɓaci rai Adeeb yace "what? rashad ?ubanme kakeyi anan?me yakawoka dakin Hulwa?me kayi mata" Adeeb ya faɗa cikin karaji yana ture fattu gefe guda tare da tunkarar rashad gadan-gadan kamar wani zaki. Rashad kuwa cikin rashin kunyarsa ,duk da yana jin tsoron Adeeb ɗin,yace" kamar ya me ya kawoni ɗalibta?nazone in dubata kamar yadda ammi tace ,kuma kaima ai...bai karasaba sakamakon wani bahagon mari da Adeeb ya ɗauke shi dashi,kafin ya dawo hayyacinsa ya ƙara ma wani marin,nan da nan hancin rashad ya fara zubar da jini,kuma Adeeb ya shaƙe masa wuya tare da haɗa shi da bango. Jikinsa banda karkarwa ba abinda yake" idan ka sake ka ƙara kallon koda inda Hulwa take ,wllh,billahi,saina illataka .wawa jaki dan iska "Adeeb ya faɗa cikin zafin rai da jin kamar ya karkarya rashad ɗin. Rashad kuwa tsoro ya gama kamashi, gashi Adeeb ya shaƙe masa wuya yana neman kashe shi.sai dukan hannun Adeeb yake akan ya sake mai wuya,yana kakari Kuka kawai fattu keyi tana daga tsaye jikinta na rawa ganin abinda ke faruwa,nan da nan jini ya ƙara balle mata sai zuba yake bul-bul yana bin ƙafarta. Da gudu nanny ta shigo ɗakin tana salati" magajin fada zaka kashe shi ,maza sake mai wuya " ta faɗa tana mai kama hannun Adeeb ɗin. Gaba daya hankalin Adeeb baya jikinsa.tsantsar kishi da tsanar rashad ke dukan zuciyarsa.sam yaki sake mai wuya. Rashad sai kakarin mutuwa yake. Ammi ce ta shigo ɗakin arude tana zuwa ta kama fuskar Adeeb tana faɗin"my prince meye hakan?zaka kashe shine sakeshi mana ,nice fa na aikoshi"ammi ta faɗa cike da tsoron kar Adeeb ya kashe rashad. Amma ko gezau Adeeb baiyi ba ,ba kuma alamun zai sake rashad ɗin. Rashad kuwa gaba daya jikinsa yayi kaishi dan ko hannunsa ma ya kasa dagawa bare ya kwaci kansa. Da jan kafa fattu ta ƙaraso garesu,tare da rungume Adeeb ta baya cikin kuka take faɗin"Hamma ka sakeshi,zai mutu dan Allah Hamma ka bari,jinina yana zuba zan mutu Hammana " ta faɗa tana mai ƙanƙame Adeeb sosai ta baya tana kuka. Sakin rashad Adeeb yayi yana mai runtse idanunsa da mugun ƙarfi,kafin ya dunƙule hannunsa ya daki bango da karfin gaske. Juyo da fattu yayi zuwa gabansa tare da ƙanƙame ta ajikinsa yana sauke wata zazzafar ajiyar zuciya. Ba tare da yayi magana ba ya kama hannunta suka fice daga ɗakin. Da gudu su ammi sukayi kan rashad daya fadi ƙasa yana ta tari,ruwa nanny ta kawo masa mai sanyi,ɗan kwalla Uba daya kafa kai saida ya shanye ruwan tass.yana sauke ajiyar zuciya da shafa wuyansa cikin azaba. Sannu suke ta masa ,kafin ammi ta kamashi suka bar ɗakin tare da nufar nata ɗakin. "Wllh ammi tunda yayi min wannan ƙamshin mutuwar akan wannan yarinyar,nayi alƙawarin gobe saina yi mata fyade mafi muni agidan nan,saina yi mata abinda ko likitoci bazasu iya ɗin keta ba Adeeb ya yawo bala'in da bazai kare ba agareshi da ma yarinyar" rashad Ya faɗa cikin azaba yana lumshe idanun. Kai ammi ta jijjiga cikin bashi kwarin gwuiwa tace "ina bayanta ɗana kayi mata hukunci wanda ya dace da ita" Ammi ta faɗa tana mai goge masa hancinsa. Azuciyarta kusa ,dariya take cike da jin daɗi tana mai cewa"haka nake son ku kasance kullum cikin masifa da tashin hankali,kaida uwaraka yanzu ma kuka fara gani,Allah ya kamu goben... To masu karatu nima dai haka nace ,Allah ya kamu goben ɗan ganin ya zata kaya. Hausawa gareku, masoya,jiya ƙunƙuni shiru ,wllh ina uzurine amma kuna raina.One luv💓💓 Anty mammy ce Mrs babi💘💘💘 Share and comment fisabilillah. More comment More typing.