Bismillahir rahmanir raheem 💎 L U'U L U'U (The diamond)💎 haisam&akhnan tales H U G U M A BOOK 03///PAGE 01 AGADEZ VILLA STREET Wani irin ginin gida ne wanda yasha banban da dukkanin gidajen dake jerarru kuma tsararrun layukan da anguwar ke dasu. Daga waje ba zaka bashi wannan martabar da kwarjinin ba,kamar yadda koda wasa ba zaka taba kawowa zaka samu cikin anihin gidan dauke da wani irin gini da tarin tsaron daya daukesu lokaci me dan tsaho kafin su cimma cikin gidan dama target dinsu ba. A hankali ya sauke babbar takardar daga idanunsa......takardar data kasance launin ruwan bawon lemo wadda ke dauke da wasu irin tarin rubuce rubuce da suka qunshi bayanai masu muhimmancin gaske. Sanye da wasu irin baqaqen kaya da suka sake bayyanat da ainihin zatinsa......kamalarsa suka kuma cikashi da wani irin kwarjini. Duk da cewa bai bada dama ga duk wanda ke tsaye a gurin ba da zaiga fuskarsa kai tsaye ba.......amma wadannan idanun......wadannan idanun dake jiqe da tarin abubuwa masu yawa da nauyin gaske........suna juyawa ne tsakanin mutanen dake durqushe saman gwiwoyinsu a gabansa. Mutanen da bai taba tunanin sune zai samu cikin gidan ba,duk da ya sani......yana kuma ji a jikinsa tabbas BINNANNUN ABUBUWA ne da zasu iya zama da nauyin da ba kowacce zuciya ce zata iya dauka ba......ya kuma sake gasgata hakan........ya sake amanna lokacin da shiga cikin gidan yake neman zame musu barazana. Daga faffadan parlor din daya zama ZUCIYAR GIDAN,kuma mahada me hatsarin gaske data game kowacce boyayyar shiyya ta gidan.....boyayyun sasannin da ba lallai ordinary mutum ya iya gani ko ya iya fahimtarsu ba. Da wata irin nutsuwa ya sauke idanunsa akan mutumin da qirarsa halittarsa da kuma salon shigarsa yasha banban data kowanne mutum dake durqushe a parlor din. "TAMIM" Sunan ya sake harbawa a kansa da wani irin tarin mamaki da kuma sake jinjina girman zaren dake daure da dukkan wata sarqaqiya. An haifa an kuma qirqirar tare da tabbatar da sunayen TAMIM har uku cikin masarautar agadez. Ba don komai ba,sai don a batar da hankalin masu hankali,a sauya nazari da hangen nesan dukkan wani me tunani a duk sanda za'a furta sunan TAMIM a masarautar agadez,ta inda dukka hankali bazai kai ba. Da wani irin sanyi ya sake zare idanunsa daga kan mutumin.......mutumin daya dauki shekaru yana wahalar da K'ASARSA......mutumin daya sanya shugabanni masu yawan adadi da suka jagoranci Security Agency dinsu suka kammala wa'adinsu.....suka kuma sauka da tarin burin shigarsa hannunsu.....mutumin daya zama silar jefa tsoro cikin masarautar OROMO.....mutumin daya yanke nutsuwa da dukkan farinciki daga ahalin AJANI AHMED. Kallonsa kawai yana rura wata irin wuta daga zuciyarsa......kallonsa kad'ai yana sanyashi yaji kamar ya yanke dukkan hukuncin daya kamata ace ya fuskanta a lokacin.....saidai kuma akwai saura......akwai kuma lokaci.....ba kuma yanzu ba.....ba'a daidai nan ba. Yanaso ya zama AIKE ga dukkan wani sassa da rassa sa sukayi tarayya wajen ginashi.....wajen gina laifukansa......wajen tabbatar da wanzuwarsa. Sau biyu yana bude baki da zummar masa magana sai ya maida bakinsa ya rufe. Baya da tabbacin komai da zaice masa.......saidai yayi imanin duk da girman jikinsa.....wannan gangar jikin da yake alfahari yake kuma taqama da ita tayi laushin da har tsakiyar zuciyarsa yasan yana ji. Artabu ne suka fara dasu beeno......daga qarshe dole muhammad haisam yayi taking over......yayi masa wata irin qofar rago ya sanyashi a corner ya shigo hannunsu. Takun tafiyar dake kusanto gurin ya sakashi maida idanunsa hanyar da sautin yake fitowa. Omar salawii da abeer ne......sai idanunsa suka sauka kan matashin saurayin dake tafe a tsakiyar su. Dukkan idanuwa haisam ya zuba masa.....kamar yadda shima matashin nasa idanun ke cikin na haisam tamkar yana neman wani abu daban.....wani abu daya banbantashi da sauran halittun dake gurin. Wannan zuciyar dake kwance cikin qirjij haisam ce ta motsa.......yana jin wani rauni yana tsarga masa. MATASHIN AMSAR TAMBAYARSA NE......fuskarsa kawai AMSA ce ga tarin tambayoyin da basu qarasa warwarewa cikin kansa game da gidan ba. AJANI qarami yake gani yana takawa da qafafunsa.......ta wani motsin nasa kuma SAFEENA ce. Shine wannan jinjirin......wannan jaririn da aka dauke tun daga ranar haihuwarsa......shine wannan yaron jini na farko.....kuma iri na farko daga jikin safeena....... Ci gaba da kallonsa haisam yakeyi,sanda suke sake kusanto inda haisam din ke tsaye. Sai yaji kaman qafafunsa sunayin sanyi a sanda yake karantar sigar yaron,don haka ya dunqule dukkanin hannuwansa yana cusasu a aljihun wandonsa yana ci gaba da qarewa matashin kallo. Idan dai har nazarinsa yana tafiya a yau a daidai......idan dai har abinda idanunsa suna iya gane masa daidai......nutsuwa da wani irin kamewa yake gani qarara tattare da matashin,abinda yasha banban sosai da AHMAD ALMAZ. Kallon kallon dake Tsakaninsu bai yanke ba,har sai da suka iso dab dasu. Da idanu ya yiwa omar magana,sannan ya maida dubansa akan sauran dukkaninsu. Su dinma da ido kawai ya musu magana suka fahimci me yake nufi,ya juya a hankali ya fara takawa,saidai maganan da tamim babba yayi da yaren oromo ya sanyashi d'an dakatawa kadan. "Ina kyautata zaton kai din jinin ABA JIFAR NE......IBRAHEEM din da qaddarar salwantar SALEEM magajinsa tazo a hannuna" Yayi maganar da qeqasashen lafazi,da kuma wannan qeqasashiyar zuciyar da a iya lafazinsa kawai ta nuna hakan. Yaji saukar maganarsa har cikin ransa......yaji saukar dukka lafuzansa gaba daya.......saidai juyawa ya kalleshi a irin wannan yanayin zai iya haifar da komai,don haka sai ya zabi ci gaba da takawa a nutse,muryarsa da wannan haibar ya furta. "Beeno.......inason a batar da gidan". Gajeriyar maganar data qunshi tarin ma'anonin da baida buqatar tsaiwa fassarawa su abdii din. A K H N A N Ba zata ce ga wani abu dake riqe da zuciyarta ba.......amma tabbas akwai wani baqon abu dake ragaita tsakanin zuciyartata zuwa qirjinta. Wani fayau takeji tsakanin zuciyartata zuwa qirjin nata lokacin data tsinci kanta da sanya karatun qur'ani bayan shuru da kad'aicin da ita ta zabeshi ya mamayi dakin......zuciyarta tana mata tuni da kalamansa na qarshe "yawan saurare da karanta alqur'ani yana sanya zuciya ta samu nutsuwa" A hankali haqiqanin yarda da maganarsa yake ratsata,wani irin yanayi me cike da nutsuwar da bata zaton akwai yiwuwar samuwarta ba ga ruhi da gangar jiki bayan fuskantar wata mummunar baraza daga rayuwar dan adam ba itace take ratsata. Sassanyan sautin nan nasa daya samu nasarar shiga kamfanonin dake sarrafa na'urar MP3 na zamani masu zuwa da fitilar gado. Wannan kwantacciyar qira'ar......wannan muryar dake nuna zallar nutsuwar da mamallakinta ya mallaka tun kafinma kakai ga ganin anihin fuskar me muryar. (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) Kamar ita dai......a yanzun da sautin karatun ke shiga kunnenta da wani irin nutsuwa da sanyi,sai fuskarsa take dawo mata......sai fuskarsa take gilma mata da dukkan wannan motsin nasa dake nuna irin izza da qasaitarsa......tun daga ranar farko a hippodrome.......a hankali har zuwa awanni da lokutan da suka samar da kusanci me girma tsakaninsu....wato festival d'lAîr......ranar da taso zame mata wata mummunar rana da zata shafe tarihinta raga SARAUNIYAR QASAR AGADEZ zuwa wata halitta mafi qasqanci. Saidai taimakon Allah,da kuma wanzuwarsa.......jarumtarsa dama wata irin zarra daya mallaka ya sanya ta kubuta daga wannan mummunan harin. A hankali ta bude idanunta da zuwansa qarshen suratul baqara wanda yayi daidai da tambayar data harba cikin kwanyarta. "Akwai wani abu da wani zai sake bata a duniya da yakai darajar abinda yayi mata?" Tambayar ta sauko mata a hankali tana hadewa da wata tambayar data sake zuwa mata. "Inda ace tamim ya samu nasarar abinda ya qudirta......inda ace abinda ya tsara ya tabbata......inda ace haisam baya tare dasu a wannan lokacin fa?.....me zai faru?. Tambayar data sake buga wani abu me girma a qirjinta,abinda ya tilasta mata lumshe idanunta a karo na biyu,saita samu labbanta ta furta. "Astagfirullahal azeem" Da wani irin yanayi da ya bayyana cikin kunnuwanta......da wannan muryar tasa......da wannan taushin a sautinsa wanda ya zama tamkar dan jagora a gareta,har zuwa sanda taji yanayinta ya daidaita......yanayin kuma da yazo daidai da fara kiran salla cikin wayarta dake ajiye a gefanta. Idanu ta zubawa wayar tana kallonts kamar me sauraren jiran wani abu,kiran sallar yana fita a nutse......irin kiran sallar da masjid haramain sukeyi kowanne lokaci na salloli guda biyar din,bata kuma dauke idanunta ba har sai da wayar ta gama kiran sallar. A hankali ta miqa hannunta ta dauki wayar tana latsawa. Shine ya sanya mata kiran sallar tun a wancan ranar daya kaita wancan gidan......wancan gida dai da batasan har yanzu ina bane?,gidan waye kuma cikin agadez. Kiran sallan da a wancan lokacin takejin ya takura mata.......saboda duk wata sa'ar da lokacin sallah ya shiga zai dameta da bugawa har sai tabar komai taje tayi sallar. Tayi dukka shige shigenta cikin wayar amma kuma ta gaza ganin ta inda ya sauke manhajar,ta kasa gane komai......ta gaza fahimtar komai. A dole ta haqura,har kuma zuwa yanzu data fara sabawa da abin. "Manzan Allah yayi jan kunne sosai game da sallah......ya gargademu mu kiyaye lokutanta,wata abace da duk kyan ayyukanka idan ka samu naqasu a kanta to bata yadda zaka wuce a gurin Allah.....komai naka.....dukkan ayyukanka sun baci......sallah kadai magani ce......tana gyaran zuciyar dan adam dama ayyukansa,idan ka kyautata sallarka to hatta da zunubai zasuyi qaura daga gareka.....amma idan har kana sallah.....kuma baka daina aikata munana ayyukan da Allah ya hana ba.....ta iya yuwuwa sallarka aslan bata karbuwa........ko batayi yadda Allah yake sonta ba,shi yasa bata tasirantu a kanka gurin hanaka miyagun laifuka ba". Ta tuna d'aya daga cikin maganganunsa da taji a wata rana da suke karatu dasu falaak. Kafin tayi kowanne motsi birra ta nemi izinin shigowa,kamar kowanne lokaci cikin girmamawa da suka saba bata ta sadda kai. "Lokacin sallah yayi ranki ya dade" Tayi maganan tana sunkuyar da kanta qasa. Idanu akhnan tadan zuba mata kadan. Karan farko da birra ta soma shigowa don tunasar da ita lokacin sallah?.......to me ya faru?......me ya kawo wannan sauyin?. Bata tsananta wannan tunanin ba,saboda jikinta dake bata daga inda canjin yazo,sai kawai ta yunqura ta miqe sosai tana zama saman lallausan qaramin gadon hutawar. "Tanti Aisa ta bayar da saqo......tace a shaida miki ta wuce......tace mu barki basai mun mata iso ba.....mu barki ki huta......amma zata dawo nan da kwanakin tafiyarku taga tashinku in sha Allah" . Ta danji mamaki kadan na tafiyar aisa din a wannan lokacin. Ba lokaci bane daya kamata ace ta tafi din ba,saboda ko kwanakik festival din basu kammala ba bare ayi shirin komawa...... "Akwai wani abun da kike buqata?" Birra ta sake fada a ladabce. Maganan yadan bawa akhnan din mamaki,har sai data waiwaya ta dubi birran. Ta sani......wani sabon abune yin kalar wannan tambayar ga akhnan din. "Afwan........umarni ne daga abdii wanda ya sameshi daga sheikh muhammad........komai qanqantar buqatarki a sanar a kuma yi abinda ya dace". Ta dauki wasu lokuta kadan tana kallon birra,maganan kuma yana samun wani mazauni na daban yana zama cikin kanta. Ba yau ne karo na farko da ake kula da buqatunta ba.....ba yau ne lokaci na farko da buqatunta suka zama abun riritawa da kulawa ba......amma a yau dinne takejin komai kaman yasha banban da yadda aka saba mata. Batace da birra komai ba ta miqe a nutse. "Ina buqatar zuwa dakin karatu na mai martaba" Ta fadi haka kurum. Haka kawai takejin tana buqatar duba wani littafi daya shafi tarihin manzan Allah. Tanason ta samu haske kan abinda ya shafi ma'aikin da yake yawan cewa yace ko yayi. A yau karo na farko a rayuwarta tana sha'awar duba tarihin rayuwar fiyayyen halitta da yadda yayi rayuwar tasa. *zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 09166221261 KO 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 09166221261 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 09166221261 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 02* "An gama" Birra ta furta sannan ta miqe,saidai kuma tadan dakata kadan. "Saidai morsa safiyya tabar saqo". Ido kawai akhnan ta lumshe kadan tana budesu sanda take qoqarin tura sumar kanta data cika mata kanta cikin siririn band. "Tace inda zai yiwu,da kin daure kin qarasa karbar ragowar gyaran jikin na kwanakin da suka rage" Kaman ba zata amsa ba......da wannan kalar miskilancin daya zame mata halitta taci gaba da takawa,har takai qofar toilet din sannan ta bada amsa kafin ta shige. "Zan shiga......bayan na kammala da library din". Haka kawai takejin nauyin a yau karon farko tace da morsa safiyya ba zata amsa tayinta ba......ba kuma zata amsa kiranta ba. Sanda ta shige bandakin saida birra ta saki qaramin murmushi kadan sannan ta juya ta fice don sanar da fitarta daga sassan nata zuwa sashen da dakin karatu na me martaba yake don a gyara hanya. Doka ce.....kuma tsari ne nata ita kadai......bata tarayyan hanya da kowa a sanda zatayi tattaki cikin gida. Duk wani kai kawo zai dakata a hanyoyin da zata wuce din har sai takai inda tayi niyyar zuwa. *_H A I S A M_* D'aure da towel ya fito a qugunsa,towel din da duka duka tsahonsa iya qasan gwiwarsa ne da kadan.....qanqantar towel din ya sanya bai rufe duk wani ginannen jiki da surar qarfi me cike da zati da cikar halitta da Allah yayi masa baiwa da ita ba. Wani yanayi da ba wanda yake bari ya ganshi a haka.....koda kuwa su omar ne. Sassalkar sumarsa dake d'igar ruwa kadai ta isa ta shaida maka wanka yayi,ya kuma kwarara ruwan daya ratsa cikin wannan sumar tasa ta anihin qabilar oromo da gasken gaske. Tun daga takunsa zuwa yanayin fuskarsa zaka karanci qarancin kuzari da kuma walwala me tarin yawa dake tattare dashi. Haka yake.....don can cikin kansa yakejin kamar ana wasu qananun tsawawwaki tun daga sanda binciken farko ya kammala akan matashin da amsar daya bashi bayan ya tambayeshi sunansa. "BANI DA SUNA" Shine kawai sunan daya sani nasa a matsayinsa na cikakken dan adam daya debi shekaru sama da ashirin yana rayuwa. "JININ AJAANI NE......JININ SULTANE MUHAMMAD HAMMUD NE" Wadannan maganganu guda biyu bayajin akwai wani lokaci yanayi ko sa'a da zasu shafe daga cikin kanshi. Ko a yanzun daya tsaya gaban qawataccen makeken madubin lafiyayyen master bedroom din nasa.......sai daya cusa yatsunsa dukka goma cikin jiqaqqiyar sumarsa. Yaja iska sosai cikin hunhunsa yana fesarwa bayan ya sauke hannuwansa a qasa. Yayi cases kala kala na criminals iri iri......yaga tarin abubuwa da suka qara qarfafar imaninsa.......ya shiga cases masu hadarin gaske,ya kuma binciko sannan ya tabbatar da gaskiyar me gaskiya.......amma bai taba ganin zallar qwarewa gurin iya cutarwa.......daukan fansa akan wanda ba ma'abocin laifin ba.......da kuma tsananin bijirewa Allah irin na ZEENATUN ZAITUNA BA. Manyan idanunsa masu wani irin kyau......irin kyan da ba abinda yake sauya sunansu na KYAWAWA ya lumshe yana sake cusa yatsunsa guda biyar cikin sumarsa gami da budesu fes saman kyakkyawar fuskar nan irin ta matasan oromo masu jini a jika. Wani irin zafi yakeji daga can cikin zuciyarsa....zafin dake farawa tun daga saman fuskarsa har izuwa gangar jikinsa idan ya tuna AHMAD jini ga akhnan.......yayanta shaqiqinta da bata da kamarshi shi ZAITUNA taso aurawa a matsayin MIJINTA?. "Ya salam" Ya fadi yana dunqule hannunsa a sanda zuciyarsa ke tambayarsa. "Inda haka ya faru fa?,inda komai ya faru kaman yadda taso fa?,inda komai ya kasance kamar yadda ta tsara fa?". Wani irin rauni yaji qafafunsa sunyi da wani irin sanyi,kamar a yanzun abun ke shirin tabbata......wani irin rauni da babu kamarsa koda kuwa a runtsin aiki cikin kalolin ayyukansu masu tsananin hatsari da sarqaqiya,sai ya fara komawa da baya a hankali yanajin kamar nauyin dake cikin zuciyarsa shine yake qoqarin rinjayar gangar jikinsa gaba daya. Yana shirin zama kiran wayarsa ya katse masa wannan hanzarin,ya sanya hannu ya dauki wayar yana duba sunan. Omar ne.......sai yanzu ya tuna ya barshi yana jiransa tsahon lokaci,don haka bai bata lokaci ba ya daga kiran yana fadi a taqaice "dhiifama,dhufaa jira(afwa,gani nan zuwa)". Omar baice komai ba kamar yadda shima bai jira yaji abinda zaice din ba ya katse wayar,saidai kafin yayi wani yunquri green light ta bashi alama. Green light ne na musamman daya qirqireshi ya kuma jonashi da duk inda yakeso yake kuma buqata cikin wasu sassa nata dama wasu sassanni na masarautar ba tare da sanin kowa ba. Cikin nutsuwa ya miqe,ya isa inda qaramar na'urar take,ya dauko wata qaramar system dinsa ya koma gefan mulmulallen gadon da yafi kama da qaramar duniya bawai gado ba ya zauna sosai sannan ya soma hada komai daidai da yadda yakeso. Hannaunsa dafe da stool din daya dora system din yake kallon komai. Ta fito sosai ta cikin allon system din sanda take takawa a nutse birra na biye da ita. Wani irin taku da zaka dauka yauqi ne ko yanga bawai dabi'a na halittarta ba,takun da cikin kowanne yanayi yake iya nuna yadda qasaita kebin jininta. Idanunsa ya zare a hankali yana maidawa gefe inda wayarsa ke ajiye,siririyar ajiyar zuciya ta subuce masa. Wayar ya dauka ya bude da nufin aika saqo,wani abu yana kuncewa daga can qasan zuciyarsa,a yanzun daya sake ganinta sai yakejin rad'ad'in da yakeji a qirjinsa ya ninku......sai wani siririn abu me me kama da tausayi dake huda zuciyarsa a hankali,yanajin kamar ya rasa wani bangare na juriyar iya kallonta na tsahon lokaci,kamar yafi buqatar tsaronta a yanzu sama da kallon nata. Bugu daya aka daga wayar,ya sakata a kunnensa. Idonsa ya lumshe ya kuma bude lokaci daya,yana jin yadda zuciyarsa har yanzu take ba dadi,cunkushe da wannan abun da yayi masa tsaye da har yanzu ya gaza fassara mene shi. Labbansa ya motsa yana amsa sallamar,wadannan kyawawan labban dake daukan hankali da burgewa. "Ina zasu fita?". "Dakin karatu obbo". "Akwai cikakken tsaro?" Kaman haisam yana gabansa abdii ya gyada kai. "Akwai obbo" Shuru ya gilma na sakanni kaman bazai amsa ba kafin yace. "Zaituna ba......inaso a zareta daga cikin jerin sahun mutanen da suke da damar ganinta kai tsaye.....koda kuwa ta buqaci hakan" "An gama obbo" Abdii ya fadi,amsawar ta abdii kuma ta kawo qarshen maganan tasu,ya maida wayar cikin nutsuwa ya ajiyeta. Miqewa yayi yayi tattaki zuwa gaban mirror din,har yanzu yana jin kansa a cushe a kuma cunkushe da tarin abubuwa. A duk sanda zai tuna matasan guda biyu......a duk sanda zai tuna abubuwan da suka shude a wannin da suka gabata sai ya sakejin bacin ransa yana ninkuwa. (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) Tsaf ya shirya cikin black trouser da dark olive green shirt. Kalolin da suka zauna da wani irin tsari da kuma dacewa a gangar jikinsa. Sun fidda tsahonsa dama murjewar murdadden jikinsa,kamar yadda suka haska farar fatarsa zuwa fuskarsa da a yau ya amsa cikakken sunansa na MISKILI ZAM. Sassanyan turaren nasa dai shine abu na qarshe daya maida ya ajiye,sannan ya fara nufar qofa da 'yar sassarfa yana fita,kaman wanda ya tuna da mantuwar wani abu me muhimmanci da yayi. Takunsa shi ya sanya Omar daga kansa daga tattaunawar kai tsaye da sukeyi da bobbo muhammad dawud ta hanyar kiran kai tsaye na ido da ido wato video call. "Gashinan bobbo" Omar ya furta a nutse yana tashi ya zauna sosai saman kujerar. Kai tsaye ya zabi daya daga cikin kujerun dake daura da omar,kuma tun kafin ya zauna ya miqa dogon hannunsa yana jawo fuskar system din zuwa saitin inda zai zauna din sannan ya koma ya zauna a dan gaggauce. Abeer ya miqa wayoyinsa tare da sign na saka masa charge kafin ya dawo da hankalinsa kan allon system din. Kan bobbo muhammad dawud idanunsa suka sauka,wanda ya zubawa haisam din dukka idanunsa da irin kallon daya tabbatarwa da haisam din nazarinsa bobbo din yakeyi. Janye idanunsa haisan yayi sanda bobbo Muhammad dawud ya saki qaramin murmushi,har yanzu idanunsa akan fuskar haisam din. "Me yasa banga alamun farincikin nasara ba saman fuskar muhammadu ba?" Ya furta har qasan zuciyarsa yana mamakin daukewar walwala daga fuskar haisam. Ba haka ya zata ba,bama shi kadai ba.....dukkan wanda yasan da aikin......dukkan wanda yasan da aikin yana hasashen farincikin nasarar haisam a ranar zai zama na dabanne. Yatsunsa ya murxa kadan,baisan me zaice da bobbo da zai gane.....baisan da wanne yare zaiwa bobbo bayani ba,bashi kadai ba harda su omar. Abu daya ya sani wani qatoton abune yake a tsaye a wuyansa a yanzu haka idan ya tuna shirin mammina mafi muni,shirin halasta haram tsakanin muharraman da tafi kowa sanin girma da nisan haramcin dake tsakanin AHMED da KHADEEJA. "Akwai sauran bayanai" Bobbo ya fadi kansa tsaye yana duban haisam. Sai a sannan haisam din ya dawo da dubansa ga fuskar bobbo din,ya gyara zamansa da yanayin zamannan dake cike da qasaita wanda ya zame masa jiki,ko a office ko a taro koma a inane,wanda yawancin lokuta baimasan yana yinsa ba. "Akwai" Ya amsawa bobbo a nutse da muryar nan tasa da nutsuwa kewa ado koda yaushe. "Ina saurare" Bobbo ya fada shima yana tattarawa haisam dukka nutsuwarsa. "Asalin sunan ZEENATU ne.....zaituna sunan aminiyarta data salwantar da ita ne bayan ta tabbatar a duniya itace kadai ta rage halittar datasan kaf sirrikanta.....ta taho da jaririn ajaani xuwa niger.......ta kuma dauki jinin sultane muhammad hammud ta maidashi tantirin dan shaye shaye bayan ta bayar da kyautarsa ga magajiyar karuwai.....kyautar da an shiryata ne da nufin za'a waiwayeta bayan wasu shekaru saboda cika wasu munanan qudure qudure da muradi na hada haramtaccen aure tsakanin 'yan uwan da aure tsakaninsu ya haramta har gaban abada.......khadeeja diyar sultane......da ahmed babban d'an sultane daya kamata ace yana rayuwa a fada yanzu kaman sarki,.......wanda ya kamata ya karbi sunan MAGAJIN SULTANE a yanzu haka" Ya qarashe maganan yana jin wani d'aci yana ratsashi tun daga zuciyarsa har izuwa harshensa. Shuru ya sake wanzuwa,girma bayanan da haisam yaci gaba da bashi yana ratsa bobbo. Girman rashin imani.....zallar zalunci da BAQAR SHUKAR zaituna yana ratsa zuciyar abbo din. "Lokaci yayi muhammad.....a yanzu ka lalata komai,ka kuma bata dukkan wani shaida makama ko hujja tata,......ka saare dukkan wani qarfi da takejin tana dashi,na baka dama a kanta a yanzu" Bobbo muhammad dawud ya fada shima yana jin wani irin abu me nauyi yana sake sauka a zuciyarsa. Wani kalar murmushi ne ya subucewa haisam din yana murza tafin hannunsa da yatsunsa,wani kalan murmushi da baida alaqa da jin dadi ko walwala ko kadan. "Taci bulus kenan bobbo" Ya furta calmly,saidai wutar dake ruruwa me girma ce. "Zunubin zama a qasar AGADEZ,cakuduwa da mutane masu aminci,da kuma ha'intarsu kadai....iya wannan zunubin yafi qarfin a kama zaituna cikin girma......dole ta rasa wannan GIRMAN data dade tana tattalinsa.......dole kuma ta zama mutum ta farko da zata fara tonawa kanta da kanta asiri........inaso a gaban idanunta AHMED ya zama magajin sultane....... Inaso akan idanunta abinda take jayayyar hukuncin Allah a kansa ya faru alhalin bata da yadda zatayi....." "Sultane fa?" Bobbo ya fadi yana duban tsakiyar idanun haisam,yana kuma karantar zurfin bacin ransa. "Za'a yi komai yana nan......saidai zai dan kwanta ya huta da kalar hutun da zai zame masa sassauqa.....hutun da zai hanashi ganin wasu daga cikin tashin hankulan da suka durfafoshi suka durfafo iyalinsa,suka koma durfafo masarautarsa......na shirya kawai bobbo.......idanu da kunnuwanka kawai nakeso ka kulle......a yanzu na shirya kowa yasan waye sheikh muhammad haisam ibraheem aba jifar......" "Al_saamit?.......the silent one?" Bobbo ya fada da wani kwantaccen kuma sauqaqqan murmushi kan fuskarsa. Ya sani,tsokanarsa bobbo yake,wata tsokana cikin girmamawa wadda haisam ya riga ya saba da ita. "Na kulle muhammad.......na damqa maka dukkan wata dama kuma dari bisa dari.....na zare hannuna na baka wuqa da dama......ka qarashe wasan da dukkan salon da kaso" Idanunsa haisam ya lumshe yana kuma budesu dukka lokaci daya. *zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 09166221261 KO 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 09166221261 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 09166221261 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 03* "Na gode" Ya furta yana kuma qoqarin shutting down system din. "Salaana ya fito da mota" Haisam ya fadi yana qarashe kasheta ba tare daya dubi omar da yakeson yayi tambayoyi wa haisam din ba. *M A M M I N A* _"Kwanciya ba taki bace zaituna........ki tashi zaituna.......ki tashi ki nuna ma koma waye da yake wasa da rayuwarsa cewa yana kutsawa sansanin mutuwa ne yana yin wasa da ajalinsa......ki tashi zaituna kada ginin nan na shekaru masu yawa da kika jima kina yi ya fado ya danneki.....ki tashi zaituna!!!.....kada ki bari akhnan ta fahimci komai.....kada ki bata qofar da zatayi nisa dake da burikanki ba tare da sun kammala cika ba"_ Ire iren wadannan maganganun sune abinda taji zuciyarta na rad'a mata har cikin kunnenta a sanda take kwance da tarin zazzabin da ya dinga kadata kamar zata datse harshenta da haqoranta. Wani irin wuf tayi ta tashi.......ta kuma buqaci maganin da zai warkar mata da zafin zazzabin cikin mintuna goma ko ashirin. Ta karba ta kuma sha,sannan kuma ya sauka kamar yadda tayi buri,ta shiga tayi wanka,sannan ta buqaci abinci wanda ta zauna ta cishi sosai ba tare da tana banbance d'and'anonsa ba. Tana cine kawai saboda tana buqatar energy sosai a tattare da ita,tana cine saboda tana buqatar aga confidence da cikakken karsashin nan da aka santa dashi,tanaso ta fito a giwarta sak,batasan komai nata ya nuna karaya ko rauni. Ta sani......indai cimmawa ne an riga da an cimmata.....ta sani,jikinta kuma yana bata akwai tarin baqin fuskar dake rayuwa cikin gidan.....akwai tarin inuwoyin da suka saje da duhun katangun gidan,suke rayuwarsu suna kuma farautarta ba tare data san hakan ba,saidai koma waye.....koma meye tana bawa kanta tabbacin indai itace wannan zaituna din.......indai itace zeenatu to sai ta sanya nadama a zuciyar dukkan wanda yayi gigin ketawa ta cikin shirin ta......rayuwarta dama dadadden burinta. SHIEKH MUHAMMAD HAISAM sunan da yake kwance a ranta......sunan daya zame mata tamkar wani jarrabawa. Dashi take kwana.....dashi take tashi.......tare da dukka tsare tsaren yadda zatayi dashi,ta yadda ba wani malami da zai sake mararin shigowar masarautar AGADEZ yace zai rayu ba tare da amincewarta da samun dama da dukkanin goyon baya daga gareta ba. "Ki aika saima....ta duba cikin bangaren suturu mafi zama alfarma ta bani daya" Tayi maganar da d'aya daga cikin hadiman da ita ke biyewa yalwa a matsayi a gurinta. Har hadimar ta fice idanunta yana kallon sashe daya,lissafinta akan toshewar kowacce qofa da zata bada makama akan batan yalwa takeyi. Ba yalwa ba dalilinta,saidai ba wani abu da zai alamtawa kowa b'ata yalwan tayi,b'atan nata yabar tarin hujjojin da duk wanda ya kalla zaice yalwa ta zabi ta tafi da qafafunta bawai da sunan b'ata ba. Ta sani......ta kuma tabbatar da cewa. Bata yadda za'ayi yalwa ta zabi tafiya daga gareta,bata yadda za'a yi yalwa ta zabi tafiya daga masarautar agadez. Tafiyar yalwa din wani SHIRYAYYEN ABU NE da mutane irinta ne kadai zasu gane hakan. Tsaf ta shirya cikin ire iren shigar dake nuna zallar alfarma alfahari da kuma izzar da takejin tana da ita. Ba kwanaki ko shekaru qalilan ba........a dukka tsahon shekarun data kwashe qasar agadez ta samu wani irin girma da ba wata halittar diya mace data sameta. Girmamawa da tarin darajtawar da ita ta nemeta.......ita ta siyeta.......ita kuma take tattalinta har kawo yanzun da takejin ba wani.....ba kuma wani abu daya isa ya rabata da wannan izzar tata,izzar da itace MAKAMINTA izzar da takejin zatayi dukkanin me yuwuwa gurin adanata da kyau har zuwa sanda numfashinta zaibar gangar jikinta. "Ina fatan akhnan na cikin gida?". Kai ta gyada mata cikin maqurar ban girman nan da suka saba bata. " Eh tabbas.......ance ta fita zuwa dakin karatun me martaba" "Dakin karatu kuma?" Mammina tayi tambayar tana zubewa hadimar tata idanu. "Eh Allah ya baki yawan rai" Shuru ya ratsa kadan,mammina din tana juya zoben dake yatsar hannunta. Wani abu ne yake harbawa cikin kanta da saurin gaske yana sake nauyayawa da kuma zurfafa tunaninta. Zuwa dakin karatu baya cikin dabi'a ko al'adar akhnan din kaf tsahon rayuwar data raineta a kai,idan dan zamanta dashi ne fa?......idan dan kebancewar da tayi dashi ne wanda duka duka idan aka lissafesu guri daya ba zasu haura kwanaki biyar ba fa?. Hakan na nufin zai zamemata wani sabon aikin kenan wajen kawo qarshen alaqarsu da aurensu?. Ya kamata ta bari irin hakan yaci gaba da wanzuwa?,har takai sun fara musayar wasu dabi'u a tsakaninsu ita dashi?. "Inason magana da ita.....zan isa zuwa dakin karatun inaso kuma kowa ya sani" "An gama" Ta fada cikin girmamawa ta juya ta ficewa. A yau fitar tata ta zama cikin salon da takanyi amfani dashi lokuta da dama. Wata irin tafiya tsakanin sassanta zuwa dakin karatun sultane din. A kowanne taku da zata gamu da bayi ko hadiman gidan kyauta ce take yinta. Kyautar kudade ga duk wanda suka hadu a hanya dashi. Wannan salon yana daya daga cikin wani hanya data bata daman mallakar zuciyar mutane da yawa dake rayuwa cikin masarautar,alkhairinta kuma ya danne na kowa........sai d'ai d'aikun da har a lokacin alkhairin nata ya gaza saya mata matsugunni a ransu ba tare da suma sunsan dalili ba. *_SHEIKH MUHAMMAD HAISAM_* Cikin lafiyayyar motar Mercedes Maybach S_class suke tafiya zuwa killataccen gidan dake cike da tarin tsaro. Killataccen gidan da almaz ya dade a cikinsa.......JINJIRI da har yanzu baida cikakken suna kuma D'A ga ajani ya zama cikon na biyun. Yana zaune d'ai d'ai saman lausassar kujerun alfarmar da motar ta mallaka,yayi relaxing sosai cikin kujerar,dukkanin idanunsa a lumshe suke qasa qasa,zaka iya dauka bacci ne yake shirin saceshi. Sau uku omar yana daga idanu yana dubansa,sai ya bari ba tare da yace dashi komai ba. Iya yanayinsa kadai ya gaya masa 'yan miskilancinne suka motsa,dukkan alamu sun nuna bayason magana me zurfi....kaman yadda yake ganin alamun akwai wani kwantaccen fushi qasan ranshi. Tafiyar kusan awa daya ce cif ta kaisu unguwar,unguwar dake a wani muhalli da ba kowa yake samun sukunin zama a gurin ba. Unguwa ce ta masu hannu da shuni dake cikin garin agadez qwarai da gaske,wannan ya sanya unguwar keda wani irin security sosai. A hankali omar ya dafe Bluetooth din dake kunnensa sanda suke fitowa daga cikin motar suna dosar ainihin cikin gidan. "Ina captain?,na gaza samunsa a waya" Maleek ya fada cikin yaren oromo. Saida omar ya saci kallon haisam kadan,yadda yake takawa d'ai da wannan ginshirar tasa sannan ya maida dubansa (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) "Kabi captain a hankali,abubuwanne yau suka motsa......da alama kaman a kusa yake,na kasa gane meye haka me girma da nauyi daya taba ransa". "Please omar.......ka fada masa" "Nooo maleek......ba'a irin wannan lokacin ba" "When?" Maleek ya tambaya cikin sarewa. Kaman omar zai saki dariya sai ya daure. "Inde falaak ce na tabbatar haisam bazai bari ka rasata ba,tunda ya tabbatar kana sonta" "I trust you......" "Kaman yadda nayi trusting Captain namu....." Omar ya amsawa maleek yana yanke kiran da dan hanzari ganin suna dab da shiga ainihin qofar farko da zata sadaka da sassannin gidan Gaba kadan omar ya qara yana daidaita tafiyarsa data haisam din,sannan ya sanya key din hannunsa ya murza ya bude qofar. Qawataccen parlor ne da aka yiwa wani sassanyan tsari me daukan hankali. Daga cikin parlor din ba kowa sai mutum uku,sheikh Ousmane ahmad(almaz),sai jinjiri dake zaune saman daya daga cikin lausasan darduman dake shimfide a qasan gurin. Idanun haisam a kansu su dukkaninsu,yayi sallama da muryarnan tasa ma'abociyar kwarjini,sallamar data ratsasu dukkaninsu suka kuma daga kai suna kallonsa. Da murmushinsa ya taso,Ahmad almaz,wanda dukkanin kamanninsa suka juye zuwa na wani kamilin matashi wanda ainihin kamanninsa na ba'abzine mallakin qasar agadez ta fara tsatsowa. Wani irin kamala da bata da alaqa kota kusa kota nesa da wancan ALMAZ din,wancan almaz din da zaituna ta sassaqashi da kalar tunaninta da cutatarwarta. Yana sanye cikin ainihin kayan gargajiya na agadez,wanda hakan ya taimaka qwarai wajen sake bayyana kamanninsa da mahaifin sultane wato kakansa. Wata irin boyayyar kama da me nazari zai saurin daukota daga fuskar almaz din. Cikin girmamawa da nutsuwa ya rusuna yakewa sheikh haisam barka da zuwa. Haisam din ya amsa yana duban fuskar almaz din. Ba abinda yake dawo masa sai wahalar da sukaci kafin su maida almaz din cikin hayyacinsa. Ba abinda yake tunawa sai ranar da sakamakon gwajin DNA na almaz ya fito,wanda ya sake wanke masa kokwanton da yayi saura a ransa na kasancewarsa jinin SULTANE MUHAMMAD HAMMUD. Ba abinda yake sake tunawa sai yadda almaz din ya birkice a sannan,kuka wiwi.....yana iya tuna kalaman daya gaya masa a sannan. "Ba ragontaka sam a tattare da d'a namiji......d'a namijin ma daya amsa sunan YARIMA kuma sarkin gobe.......idan wannan yariman yayi kuka yau.....a gobe mai zai gayawa mutanensa game da JARUMTA?" Yanayin yadda maganan tayi tasiri nan da nan a zuciyar ahmad ya sanya haisam lumshe idanunsa a hankali,ba shakka akwai wani burbushi ko kuma ace jinin sarauta sosai dake zagayawa cikin jikinsa. Idanunsa ya daga yana dorawa akan JINJIRI da yaketa tunanin bashi suna. Ba nasabarsa kawai suka datse ba......ba rabashi da mahaifiyarsa kawai sukayi ba......ba nonon dake kasancewa abinci ga kowacce sabuwar haihuwa suka haramta masa ba. Aah......daidai da SUNA sun kasa bashi.....RAI kawai suka bar masa,amma sun kashe dukkanin rayuwarsa gaba daya. Murmushi kadan ya saki,Shima ya taso a nutse zuwa gurin haisam din. Cikin nutsuwar da yake gani tun ranar farko tattare dashi ya soma gaidashi. Shi din SAK jinin AJANI.....yana diban kamanni qwarai da wasu daga cikin 'yan uwansa wadanda kamannin ajani suka dauko. Baida shakka tantama ko kokwanto akan sahihancin zamansa halastaccen dan ajani saboda komai nasa ya nuna hakan. Hannu ya miqa masa kai tsaye,miqa hannun daya lura cewa ya yiwa jinjiri nauyi har sai daya kalli tattausan farin tafin hannun haisam sannan ya maida dubansa ga idanunsa. "Karbi mu gaisa......muhammad......daga yau zaka amsa sunan muhammad" Wani abu ya gani sosai cikin idanunsa,wani irin rauni da laushi,kaman ma hawaye ne kwance cikin idanun nasa. Sanda tafukan hannunsa suka hadu dana haisam sai ya kasa boye abinda ke cikin ransa. "Tunda na tashi a jikina nakejin wannan rayuwar ba tawa bace,tunda na tashi na tabbatar akwai wani boyayyen abu cikin rayuwata,a jikina nakejin ni dinnan bani bane,ina dadewa cikin tunani,ina jimawa cikin nazarin da bansan wanda zai fahimtar dani ba,bansan fuskar kowa ba sai ta matar da tamim dana kwashe shekaru ina ganinsu tare tun tasowata......tun daga ranar dana fada hannunka na fara jin kamar sabon ruhi dama gangar jiki ka bani.....muhammad.....sunan yayimin dadi.....kaman wani suna ne me girma ko?" Ya qarasa maganan yana danyin murmushin da yafi kama da yaqe,idanunsa akan fuskar haisam. Har cikin jininsa yaji wani abu ya zarta masa,sunan annabi guda......annabin da sunansa......jarumtarsa......shahararsa da mu'ujizarsa ta zagaya ko ina,amma yau sai ga wani diyan da aka Haifa cikin musulunci da sunnar annabin baida koda labarin sunan annabinsa?. Sai da yaja iska sosai yakaita har hunhunsa sannan ya fesar,yayi qoqarin daidaita nutsuwarsa yana dafa jinjiri da ya zama muhammad ajani a yanzu. "Ba rayuwarka bace wannan.......ka kuma fita kenan a cikinta" Yayi maganan yana jin shima tasa zuciyar tana wani irin tsagewa. Wato har gwara ahmad almaz kenan?,wato har gwara gwara shi?. Shi sun barshi yaci gaba da shaqar iskar rayuwa da cakuda da mutane,duk kuwa da cewa iskar gurbatacciya ce......gurbayacciyar iska ce dake cutarwa gami da naqasa dukkanin wani gaba ta dan adam......amma muhammad fa?,sun kasheshi ne ba tare da sun zare numfashinsa daga ruhinsa ba,amma dukkanin wani kisa na ma'ana sunyi masa shi. Sun watsar dashi ne kawai yana rayuwa irin rayuwar dabba,wadda batasan komai ba sai abincinta. Ba asali......ba suna.....ba makomar rayuwa......ibada da addini duka babu ko daya. *zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 09166221261 KO 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 09166221261 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 09166221261 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 04* A nutse dukkaninsu suka zauna,ya kuma maida hankali ga oustaz Ousmane suka gaisa,sannan ya fara bibiyar yanayin karantarwar da ya dauki nauyin ya dinga yiwa ahmad da Muhammad(almaz da jinjiri). A nutse yake sauraren bayanan Ousmane,yana gyada kai a hankali. Wato lamarin ubangiji girma gareshi,duk da sun datse dukkan rayuwa daga gun muhammad amma hakan bai sanya ya tashi a wata fandararriyar halitta ba. Yanayin yadda Ousmane ke masa bayani sai ya dinga duban fuskokinsu a hankali. Dukkaninsu suna da wata baiwa ta kaifin basira saurin fahimta da daukan abu,abinda ya yiwa haisam dadi kenan,ya kuma tabbatar masa komai zaizo musu da sauqi har fiye da yadda yake zato. Kwanakin barinsa agadez ne kawai yakejin zasu haura,wasu kwanaki bakwai din yana zaton suna iya qaruwa,don yanason kafin yabar agadez ya kafa harsashi......ya kafa nakiyar da zata tarwatse da mammina dama dukkan wanda yake rab'e da ita. "Dr Na'eem ya qaraso fa" Omar yace da haisam wanda dukka hankalinsa yake kan bayanan Ousmane. Idanunsa da sukayi wani irin laushi ya daga kadan. "Ka qaraso dashi" Ya amsa yana maida dubansa ga oustaz Ousmane. "Zanga baqo,kuna iya ci gaba,bayan nan zan gansu daya bayan daya" "Mintuna goma ma suka rage mana lokacin tashi yayi......sai kuma karatun dare" Oustaz Ousmane ya fadi. A nutse haisam din yake bin wata qofa da zata sadashi da wani parlor din na daban,ya sake zube hannuwansa a aljihun wandonsa yanajin yadda jikinsa yake amsawa. Results ne na DNA test da ya bayarwa Dr Na'eem din don qara rufe dukkan sauran hojjin da kuma sake tabbatar da nasabar almaz da sultane.....muhammad kuma da ajani. A tsaye ya samu likitan,baqi kakkaura kuma giant ba'abzine sosai wanda yake da kyakkyawar alaqa da hukumomin sirri na tsaro na qasar Ethiopia. Hannu suka bawa juna kafin kowannensu ya nemi gurin zama,sannan Dr Na'eem din ya miqawa haisam wasu takardu. Baice komai ba ya sanya hannu ya karba,ya bude ta farko yana duba bayanan. Bayanan dai da zuciyarsa keta gaya masa ne na za'a samu.....su dinne kuwa rubuce saman takardar. Dukkanin qwayoyin halittar muhammad na ajani ne......komai na gwajin yazo sak da sak da ajani dama duk wani yaro daya fito daga tsatsonsa. Ta baya ya miqawa omar takardar,ya bude sakamakon ahmad almaz. Wannan karon wani huci ya sauke,ya ajiye takardar a gefe yana daga risunannun idanunsa yana duban Dr Na'eem "Na gode qwarai da qoqarinka na kawo gwajin haka da wurwuri,ina fata nan gaba idan wata buqatar ta sake tasowa zan samu goyon baya". Murmushi Dr Na'eem yayi yana duban haisam "Aiki dakai wata babbar alfarma ce ga mutum........a shirye nake koda yaushe da amsa kiranka". Sai suka sake bawa juna hannu,Dr Na'eem ya miqe yana daukan briefcase dinsa. Zagayowa omar yayi wani rudani yana bayyana saman fuskar sa,ya zauna sosai gaba haisam yana shafa sumarsa yana jin kwanyarsa na rikicewa. "Ya akayi dukka zatonka da hasashenka suka zamo daidai?.....wacce irin matace wannan mara imani?,wannan aikin......koda namiji ne ya sarqa wannan qullin lallai ya cika baqin azzalumi.....waye yake raba uwa da 'ya'yanta idan ba Allah ba?......wanne irin zalunci ta yiwa wannan baiwar Allahn?" "Ka dauka a banza Allah ya jarabceta itama ya hanata haihuwa?" Haisam ya furta da wani laushi yana qoqarin controlling kansa. Ya sani inde wannan fushin yaci gaba da masa jagora......tabbas zuciyarsa ba zata bashi goyon baya ya yiwa mammina yanayin kamun daya shirya zai mata ba. *A K H N A N* Karo na farko a rayuwarta data fara lura da irin girma da tsaruwar da dakin litattafan mahaifin nata ke dashi,duk kuwa da cewa tunda ta taso a gidan tasan da zaman gurin,amma ko sau daya bata taba mararin shiga don buqatar karatu ta qashin kanta irin wannan ba. Yau sai gata kace kace cikin dakin karatun sultane din,da wai kuma buqatar yin karatu......karatun da a yanzun takejin ra'ayinta ya karkata sosai a kansa. "Wanne littafi kike buqata ranki ya dade?" Mai hidimar kula da dakin karatun ya tambaya cikin girmamawa. Cikin izzar nan tata ta numfasa kadan. Me zata ce masa tana buqata?,littafin da zai nuna mata inda sheikh muhammad haisam ke kwaikwayon dabi'unsa?,ko kuma zatace masa tana sha'awar karanta halaye da dabi'u manzo saboda yawaitar jin abubuwa daga bakin haisam?,ko kuma dai dukka a ture wannan.....dabi'un wani d'a namiji takeson haskawa da kyau cikin kanta.....d'a namiji......malamin addini....wanda ya karya komai da komai nata......ya rushe duk wani tsari nata da komai?. "Tarihin rayuwar manzon Allah.......rayuwarsa da mu'amalarsa da kowa" Tayi maganan kaman wadda ta zabi jera kalaman kafin ta furtasu. "An gama" Ya fadi yana juyawa da dan hanzarinsa zuwa inda tarin litattafan ke ajiye jimgim amma a tsare kwaba bayan kwaba. Zamanta ta gyara sosai tana harde hannuwanta a qirjinta. A nutse da kuma wannan blue eyes din nata takebin dakin gaba daya da kallo. A hankali sai taji yadda littattafai suka cika dakin da wani irin tsari abun yana burgeta. Ba zatace ga abinda akeji a karance karance ba,idan ka dauke karatun daya wuce na magazines da newspaper da zataga sauka da tashin hannuwan jari ba. "Ga wadannan Allah ya taimakeki" Ya furta yana ajiye mata books din a gabanta. "Sunyi?" Ya tambayeta yana fatan zabin nasa ya burgeta. "Kana iya tafiya,ka shaidawa birra ta zama a kusa" Ta fadi tana aza kyawawan blue eyes dinta saman cover din littafin farko. "Le prophéte de I'Islam,sa vie d'aprés les sources les plus anciennes" Sunan marubucin ta duba "Martin lings" Saita sauke zuwa littafi na biyu. "Muhammad viedu prophéte" Ta sake duba author din. "Taariq ramadan" Ta sake zameshi qasa tana duba na uku. "La Vie du prophéte muhammad na ibn kathir" Guda daya ta zame a ciki,ta ajiyeshi gefe sannan ta gyara zamanta sosai ta fara duba wallafar taariq ramadan. A nutse takebin littafin da aka wallafashi da yarenta na faransa,cikin qasa da mintuna ashirin tarihin ya fara shiga jikinta sosai. Komai na cikin tarihin ya soma daukan hankalinta,a hankali ta soma jin wani girma da karramawa na musamman da kima na manzo yana shigarta. Sam sam komai da takeji cikin tarihinsa da mu'amalarsa bata taba saninsu ba,bata taba sanin da akwaisu ba. To yaushe ma ta zauna tayi wani karatu daya shafi wannan bangaren ballantana taci karo dashi?. Batasan lokaci yaja haka ba,saida taji sallamar birra tana neman iznin qarasowa inda take zaune. Ajiyar zuciya ta saki,tana zare idanunta daga kan littafin da takejin ba zata iya tashi a wajen ba saita kammalashi duk da yawansa,ta dora kan birra. Tsaye birran take dauke da tea tray daya bawa cups da kayan saman kai daman zama sosai a samansa,wani irin tea tray da koda tsautsayi yasa wani abu ya zube bazai zuba a qasa ba ko a jikin me amfani dashi ba,wani abu dake maqale daga qasansa ya tare wannan. Idanu ta zuba mata ba tare da tace komai ba,yayin da birra din ke dubanta da girmamawa "Allah yasa ban katsekk ba......na kawo miki wani abune,bansan ko zaki buqata ba" Kanta ta daga mata a hankali da sign din daya bawa birra daman fahimtar tana nufin ta qaraso ne. Saita tako a hankali tana ajiye tray din saman table din da akhnan ta ajiye hannuwanta akai. (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) Fidda butar shayi daya da cup tayi tana qoqarin zubawa akhnan shayin,saidai kuma muryoyin da suke jiyowa daga wajen library din ya dauki hankulansu gaba dayansu. *MAMMINA* Dukkanin idanuwanta ta zubewa hadimim tana kallonsa,kallo iri daya amma mai dauke da tarin ma'anoni da mamaki zallarsa. Wayeshi cikin hadimai?,batasan fuskarsa ba sam........abu mafi muni da firgitarwa ita GIWA ita GIWAR AGADEZ?......GIWAR SULTANE?......yau ita akewa iyaka da shiga wani sashe na masarautar agadez?. Cikin yaye yayen Mafarki ne?,ko kuma zahiri ne idani biyu take?. Wanne irin lalacewa tayi da har wani wulaqantaccen hadimi zai tsaya gabanta?,zai tsaya gabanta yana gaya mata.....yana bata labarin wani qasqantaccen malami dake ci qarqashin ALFARMARSU ya hana kowa zuwa gurin da akhnan din ke zaune har sai ta tashi?,ya hana kusantar inda take?. Akhnan din data raineta a tsakanin hannuwanta irin rainon da taga dama?. Akhnan din da ita keda alhakin yankewa komai da kuma sarrafawa cikin rayuwarta?,akhnan din da sai wanda taso ta girmama zata girmama?,sai wanda taso ta mutunta zata mutunta?,sai wanda ta lamuncewa sannan zatayi mu'amala dashi?. "A kiramin me wada" Ta fada da wani irin zafi da mamakin da har yanzu kanta ya gaza daukan itace yau a tokare a hanya,an hanata qarasawa zuwa ga akhnan. "Ranki ya dade.....koda me wada yazo ba abinda zai iya canzawa" Ya fada a tausashe yana qoqarin bata girmanta gami da rusunar da kansa qasa. "Wanene kai!.....nace waye kai don ubanka?,waye ya tsaya maka?" Tayi maganan da hargagin daya zama sanadin isar tarwatsin ga kunnuwan akhnan da birra dake cikin dakin karatun. "Gaba salamun baya salamun....Allah ya huci ranki,kibi komai a hankali karki tarwatsin da zai janyo hankulan wadanda basusan ma me yake faruwa ba.......yaduwar labarin kamar raguwar darajarki ne a idanun kowa". Tafisu ta fada da murya qasa qasa. Waiwayowa tayi tana zubewa tafisu wani irin kallo,yadda tafisun tayi mata magana saiya mata kama da wanda ke mata gatse......sao takejin kamar akwai wani sauti cikin muryar tafisu,to amma kuma can cikin kalamanta akwai GASKIYA,ba zataso kowa yasan wannan tozarcin ba sam sam,don haka ta maida dubanta ga hadimin,saidai kafin tace wani abu me wada ya qaraso. "Yaushe ni giwa na zama wulaqantacciyar da ganin d'iyata ma saida izinin wani maras darajan malami?" Maganan ta yiwa me wada zurfi da yawa,to amma ya sani,a halin da ake ciki yanzun ko sultane bazai zame mata tsanin da zataga akhnan kai tsaye ba yarjewar haisam ba. "Kiyi haquri Allah ya baki yawan rai......ba wata hanya ta tayar da maganar sheikh muhammad haisam a cikin gidan nan" Idanu ta zubawa me wada cikin madaukakin mamaki,yaushe abubuwa suka girmama haka ita zaituna tana zaune?,yaushe zamanin da bawa da hadimai dama baqi zasu iya jayayya da umarninta gami da tayar da hukuncinta?. "Karkice zakici gaba da jayayya dasu,ba tsaranki bane giwa......abu daya ya rage,kin isa da gimbiya,kisa a shaida mata zaki shigo gurinta,koda basuso idan ta aminta da haka dole su baki dama". "SU BAKI DAMA" maganar ta maimaitu cikin kanta ta kuma sanyata hadi wani abu me tauri cikin maqoshinta. Yau ita ke neman DAMA cikin masarautar?,damar da ita ke rarrabata ga wanda takeso?,ta kuma karbeta daga hannun duk wanda hakan yayi mata?. "Ku shaida mata inason ganawa da ita" Tayi maganan tana jim alwashin cewa.......yadda ya soma da qoqarin maidata maqasqanciya bayan ya fara karbe ikon zartarwa da fada aji daga hannunta......lallai ba shakka saita sanya ya dandani radadin tozarci......saita sakashi yabar agadez a mafi qasqancin halitta......barin da bazai sake koda marmarin rubuta sunan yankin ba ballantana ya kalla ko yayi mararin shigarsa. Bai musa ba,ya kuwa aika daya daga cikin masu tsaron gurin. Daidai lokacin da akhnan din ta maida labulen ta rufe... Labulen daya zama iyaka tsakaninta da gano fuskar mammina. Haka kawai takejin ta fice fit daga rayuwarta,haka kawao takejin bata buqatar karbar hanyar rayuwa daga hannun kowa.....haka kawai takejin bata buqatar shawarwari masu dogon sharhi ko fashin baqi......haka kawai takejin ta jefata rami ta goga mata tabon da har ta tsufa bazai shafe daga rayuwarta ba. Saki....sakinma irin na wulaqanci......sakin aure cikin kwanaki uku kacal da daura auren?. "Bana buqatar ganawa da kowa a yanzun......ina da abubuwa masu muhimmanci da nakeyi" Abinda ta fadawa birra kenan,ita kuma birra ta juya ta isar masa da saqon......shi kuma ya juya yana shaidawa zaituna bisa tarin qwarin zuciya da sauyin dabi'u da aka musu na FADIN GASKIYA YADDA TAKE daga rainon sheikh Muhammad haisam. Tamkar gunki haka ta tsaya a gurin cak,idanunta suna qanqancewa zuwa ciki ciki,tana jin wani tarin qasqanci da tozarci yana baibayeta. *Akhnasaim tales*🤍 *zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 09166221261 KO 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 09166221261 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 09166221261 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 05* Lokaci na farko mahaukaciyar tsanar da takewa yarinyar ta taso mata. Karom farko da wannan tsumammiyar tsanar ta yunquro daga muhallin da taketa ajiyarta ta kafa sabbin rassa da sansani......saidai wani qaqqarfan sashe na zuciyarta yana sake jaddada mata. "BA YANZU BA......DA SAURAN LOKACI" Da gaske ne......ta yadda da sauran lokaci......don ba zata taba yadda yarinyar taci bulus ba.......FANSAR SAFEENA da kuma rainon data yiwa MAQIYIYA na wadannan shekaru dukka saita fanshe......komai runtsi,komai tsanani......kuma komai wahala. "Basai kin biyo ni ba" Tace da tafisu kai tsaye tana juyawa zuwa hanyar da zata sadata da sassan sultane. A nutse ta shanye tea din da takejin d'an d'anonsa ya canza sama da wanda ta saba sha. Ya mata wani irin dadi da har sai datace da birra dake shirin juyawa ta bata guri. "Wanne irin kaya kukayi amfani dashi a coffee dinnan?" Murmushi kadan birra ta sauke,sannan ta rusunar da idanunta. "Yaukam bazan iya amsa tambayarki ba.....saboda komai ya fito daga hannun sheikh muhammad ne,yasa an kwashe komai an zuba nasa,bansan sunan coffee din ba". Shuru ta danyi kadan tana kuma karantar yanayin birra qasa qasa. "Shugaba ne.....me kulawa da dukka wani nauyin dake kansa" Wata zuciyar ta rada mata maganar. "Amma hakan shine tabbacin ya cancanci samun kusanci da zuciyarki da rayuwarki?" Ta yiwa kanta tambayar da amsarta ta tsaya cak cikin iska tana lilo. Tana jin ficewa birra,a hankali ta bude littafin tana ci gaba da karantawa,wanda dukkan wani sakin layi da zatazo sai ya aje mata points da abubuwa masu tarin yawa. *_S U L T A N E_* Cikin kasala ya sauke numfashi cikin qawataccen dakin hutawar tasa,ya lumshe idanunsa sannan ya budesu duka lokaci guda. Ya rasa dalilin daya sanya yakejin irin wannan kasalar me qarfin gaske haka a jikinsa cikin satin gaba daya. Kamar dai yanzu,fita yakeso yayi,yana da zaman fada da kuma tattaunawa da wazeer dama yayan kakan morsa safiyya akan auren falaak da yace masa anje nema ta hannunsa,amma tunda ya kammala cin abincin rana komai yayi masa nauyi. A nutse ya daga kansa da fuskarsa dake kwance da mamakin wanda ya fado masa daki haka,ba neman iso ko izini,mamakinsa ya sake fadada sanda idanunsa suka sauka akan fuskar zaituna. Cikin qarfin hali ya tashi daga kashingidar da yayi ya zauna sosai yana dubanta,kallon da yake matan ya sanya gargadi me qarfin gaske qwacewa zuwa gareta. Kuka kawai ta saki,kukan da take da tabbacin yana da tasiri matuqa ga sultane din,kukan data tabbatar yana daya daga cikin abinda ke saurin karya mata shi. "Subhanallah......zaituna....ke da kanki?" Ya fadi yana daga mata hannu yana kiranta cike da mamakin abinda ya sanyata kuka. Batayi qasa a gwiwa ba ta qaraso gabansa tana zubewa,hannunta saman fuskarta kaman qaramar yarinyar tana danne hawayen dake zuba mata. Wannan hawayen ba fake bane......wannan hawayen bana qarya bane,hawaye ne na gaske,baqinciki da d'acin da taji a sanda ake shaida mata Akhnan bata da lokacin ganinta da saurararta da kuma ganawa da ita......shi ya cushe mata mafitar numfashinta. "Bansan bani da kima daraja ko martaba ba sai yanxu......bansan cewa bankai naci darajar kasancewata matarka ba......bansan wanne tozarci aka shiryayimin ba ba tare da kunya da kuma tuna cewa ni dimma UWA ce ba koda ban haifa ba.....ni din MATARKA ce ba sai a yau" Ta fada tana sake narkewa da kuka. Ba bakinsa kawai ba,shi idanunsa ma a yanzu nauyinsu yakeji,baida wani sauran energy da zai dogon jayayya ko magana da zaituna. Ya sani wasu lokutan tana da rigimar da bata da tushe,don haka ko a yanzu sai yayi saving energy dinsa ya zuba mata idanu yana jiran ta bashi cikakken bayanin abinda ya faru daya sanyata zubda hawaye haka kamar qaramar yarinya. "Yanzu lalacewata da tozartar da aka shirya yimin har takai ni da kaina saina nemi izinin ganin biftu?,har takai bani da ikon ganinta?" Ta fada tana nuna kanta da yatsarta wasu sabbin hawayen suna zuba mata. Da zaki daina kukan da nafi fahimtarki zaituna" Sultane ya fadi yana jin yadda qafafunsa da hannayensa suke sake yin sanyi. Ta fahimci da gaske fuskantarta yakeson yi din,kuma tana fatan fahimtar tasa ta zame.mata tsani da zata soma girgiza iko da isar da sheikh muhammad yake hangen ya samu. Gyara zama tayi sosai gabansa,saidai har yanzu bata har hawaye ba,duk da yadda takejin zazzabin dake jikinta yana shirin dawo mata. "Naje da zummae duba lafiyar akhnan cikin dakin karatunka......amma hadiman da aka sauya dake kula da muhimman sashe dama biftu suka gayamin sheikh haisam bai bada wannan damar ga kowa ba sai mutum biyu......ashe bana cikin mutane masu muhimmancin da sune zasu fadi wadanda ke da ikon ganin biftu ma bawai iya kadai ganinta ba?" Ta fadi muryarta tana rawa sosai. Idanu sosai sultane ya zuba mata,yana kallon yadda take hawaye daya bayan daya. Baice da ita komai ba,sai daya bata tazarar lokaci sannan ya sake daidaita zamansa. "Zaituna" Ya kirata dakasalalliyar murya da kasalar da yake jinta har jininsa. "A yau a kuma yanzu haisam ya fimu iko da biftu.......a musulunce haisam yana da ikon iyakance adadin mutanen da yakeso biftu tayi hulda dasu suma suyi hulda da ita.....bai sabawa addini ba......" "Hardani uwarta?.yatsa ni uwarta dana raineta?" Tayi tambayar cike da zallar mamaki tana nuna kanta da yatsa. (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) "Koda ni da nake mahaifinta a yanzu ya fini iko da ita" Sultane ya fada cikin nutsatsen muryar nan tasa mai cike da kamala. Saidai maimakon kamalar ta sanyata fahimtar ainihin gaskiyar maganar sultane......sai maganan ya zame mata tamkar wani baqar magana ce daban sultane yake gaya mata. "Kanason gayamin ni ba mahaifiyarta bace ta asali?,kanaso ka tunamin abinda na riga dana sanshi?.......burin morsa safiyya na dab da cika kenan?" Ta fada cikin yanayin son tada hankali,domin kuwa dama take nema....qofa take nema da zata ja hankalin sultane ya rusa wannan tsarin,ta kuma samu daman isa ga akhnan kaman yadda ta saba don ida ginin tsari da manufarta. Shuru sultane din yayi yana dubanta jikinsa na sake mutuwa da kasala,shurun da yayi ya bata daman gama fadin abinda take da niyyar fada sannan ya soma magana a nutse "Jahiltar maganata bazai qareki da komai ba zaituna sai bacin rai.....da kyakkyawar niyya da manufa me kyau ya kamata ki kalli maganata.......ina miki bayanin nan ne badon na amintar dake ba,sai don na baki haske. A irin abinda akhnan ta fuskanta..........farmaki daga mutum mafi kusanci da aminci daga cikin masarautar mahaifinta......bazai zama abun mamaki ba don mijinta ya killaceta daga kowa ciki harda ke,ba kuma da manufar yana tuhumarki bane ko zarginki.......aah.....qilan yayi hakanne don ya sama mata nutsuwa da dawowa hayyacinta daga firgicin data fada" Ya qarasa maganar yana nazarinta. Shuru tayi,shurun kuma da bai masa kama da shurun wanda ya gamsu da maganar da aka gaya masa ba. "Me ya tashi hankalinki haka zaituna?" Sultane ya samu kansa da qare mata kallo gami da jefa mata tambayar,tambayar data zowa mammina da wani irin bazata,bazatar data sanyata daga kanta da sauri ta kalleshi,sai kuma ta buge da sharar qwalla. "Abubuwa da yawa sultane,ina tsoron kada a gina qauracewa juna tsakanin ni da ita.....diyatace......ina jinta a matsayin diyar da ni Allah bai bani ba,sai ya wanken zuciya.......ya kuma bani madadi da biftu din". Kai ya gyada a hankali. "Inde hakanne ki kwantar da hankalinki,akhnan zata cimmaki har sassanki ba tare da kin daga hankalinki ba" Kai take kadawa a hankali,yadda take kada kan a zahiri zaka dauka ta gamsu ne,zaka sauka fahimta tayi,saidai abinda yake zuciyarta......abinda ke cikin SAQAR RANTA daban yake da abinda kai kake hangowa. "Na fahimta,Allah ya saka da alkhairi" Kawai ta fadi,ta kuma zabi ta miqe. Idanunsa ya lumshe yana furta. "Madalla" Ba tare daya iya dubanta da kyau ba saboda yadda jikinsa yake sakeyin rauni. "Lokaci yayi......abubuwa sunata tabarbarewa.......abubuwa suna sake lalacewa........lokaci yayi sultane..........ya kamata na samu sarari......ya kamata komai ya qare" Abinda take fada kenan cikin ranta. Tana jin zuwa yanzu ya kamata yasan makomarsa shima.......tana jin zuwa yanzu tayi shekarun da ba wani d'a namiji data taba yi dashi.....komai izzarsa.....komai kudinsa.....kuma komai sarautarsa.......tana jin an kawo gaba.....an kuma kawo gargarar da shima ya kamata ya soma fuskantar makomarsa. "Me kika yanke?,wane mataki kike nufin dauka akan wannan abun?" Tafisu dake biye da ita a baya ta fadi qasa qasa hankalinta gaba daya yana kan mammina. Wani murmushi tayi,bawai don ta daina jin dacin abun a bakinta da zuciyarta ba.....bawai don abun ya bata farinciki ba,aah......saidon ta tabbatar ita zaituna tafi qarfin kasancewa cikin qasqantaccen yanayi irin wannan jar abada. "Lokaci yayi tafisu da sultane shima zai d'an d'ani WACE ZAITUNA kamar yadda sauran na baya wuka dandana......ya isa haka,na masa kara da yawa tafisu,lokacina ne yanzun tunda har ya fara aza matsayi da isar wasu gaba da tawa". Wani irin shuru me kaifi ya gifta kafin tafisu tace. "Me kenan ranki ya dade....?" "Ya kamata sultane ya kwanta.....ya kwanta ya huta,ya kwanta kwanciyar da zata zarce dashi har makwancin nasa na gaskiya". Maganar saita qare da wani irin shuru me wani irin kaifin gaske,tafisu ta motsa bakinta zatayi magana,amma sautin muryar hadiman dake zaune cikin wata rumfar da aka katange da bamboo wood ya ratso har inda suke. "A villa road ne.......nima dana taho daga kasuwa tun daga nesa na hangi hayaqi" "Kai kaga wutar da takeci kuwa?......me martaba bai sani ba,an jima ba'ayi mummunar gobara irin wannan ba a agadez,kuma abun mamakin gida daya ne yakeci da wutar" "Wutar nan anya haka kawai ta sauka?,lokaci guda gidan ya koma kamar burbusashen biscuit?" Dayan ya sake fadi. *Akhnasaim tales*🤍 *zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 08187255862 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 08187255862 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 06* Wata irin mummunar faduwa gabanta yayi,a hankali sai yanayin karsashin da take da yadda take daga qafafunta sukayi low a hankali. A haka ta qaraso dab da karan bamboo din,ta dakata da wani irin sanyi,sannan ta daga idanunta tana duban tafisu. "Kina jin abinda suke cewa?" Tayi tambayar kamar wadda keda hope kan tafisu tace mata bataji komai ba. "Kaman villa road ranki ya dade........" "Nan ne......jikina yana bani wani abu tafisu.......maza kiyimin magana dasu" Ta fada tana jin qafafunta kamar ba zasu iya daukarta ba,don haka ta sauqaqawa kanta,ta sulale ta zauna saman concrete chair din dake girke a gurin. A razane da jin kira daga gurin giwa suka iso,suka zube dukkaninsu kansu a qasa,zuciyoyinsu kamar zasu tsinke da fatan ba wani laifi suka aikata ba. "Ku bani labari.....me yake faruwa a villa road?" Tayi tambayar a sabule duk da tana qoqarin tattala qwarin gwiwarta. "Gobara ce.......mafi munin gobarar da aka dauki shekaru ba'ayi irinta ba......" "Ina buqatar ganin video din gurin don asan yadda za'a tari komai da biyan diyyan asara" Ta fada tana jin wani gumi yana yanko mata,can qasan zuciyarta tana sake tsananta takatatsantsan a dukka maganarta,kada ta furta wani abu da zai tona binnnan sirrinta. "Yanzun in sha Allahu zamu cika umarninki uwar gijiyarmu". Sanda suka tashi suna barin gurin bayansu tabi da kallo,tana jin kamar taje tare dasu ta gani. Gidan nan ne ya cinye da wuta kamar yadda zuciyarta ke raya mata?.....gidan nan ne daya qunshi babban sirrin da bata dashi a duniya gaba daya kamar yadda jikinta da zuciyarta suke bata?,ko kuwa hasashe ne kawai na zuciya. "Ina tamim qarami?" Ta jefawa tafisu tambayar tana jin tashin hankalin da bata taba jin irinsa ba a kaf rayuwarta,bacewar tamim a karom farko tun bayan faruwarta taji ya zame mata barazana,irin barazanar nan me wawakeken gibin da ba wani abu da zai cikeshi. Sanda tafisu ta motsa da niyyar cewa wani abu takun da sukaji daga bayansu ya sanyasu waiwayawa gaba dayansu. Idan akace mata anji qugin da cikinta ya debo tun daga qofar gate na farko na gurin ba zatayi yunqurin qaryatawa ba ko sau daya. Iya abinda take gani cikin fuskar tamim kawai qarami kawai ya gaya mata cewa yau tana fuskantar rana mafi muni cikin rayuwarta. "Ranki ya dade......gidan villa ya qone......ba alamin burbushin me rai......ba babana.......ba kowa cikin mutanenmu" Ya fadi yana kecewa da wani irin kuka tamkar qaramin yaro. "Gidan villa?,wanne gida ne a villa din dani kaina bansan dashi ba?" Tafisu ta tambayi kanta da kanta,saidai sanda tayi nufin maida dubanta kan mammina ko zata samu wani haske game da gidan........saita tsinciki miqewar mammina din da wani irin hanzari,miqewar kuma da tayi daidai da debeta da jiri yayi,ba zaton tafisu ba zaton tamim qarami ta tafi luuu gefan fuskarta ya daki kujerar. Banda tafisu tayi zafin naman tareta ba abinda zai hanata ta sake kifawa taci da baka. Cikin tashin hankali tafisu ta riqeta sosai tana kiran sunanta a jejjere hankalinta a matuqar tashe. Duk da cewa ruhinta dama dukka hankalinta suna shirin yin qaura daga ainihin wannan duniyar da muke ciki amma hakan bai hanata tunawa da makomar abubuwa masu dama data binne cikin gidan ba. "Tamim babba wanda da bayyanarsa gwara alqiyama ta tashi gaba daya......gwara a tattara a wuce zuwa filin hisabi zaifi mata sauqi......JINJIRI da har yanzu bata gama tsaida matsaya akan rayuwarsa ba......duk tana jagwalgwalawa gami da juya akalar rayuwarsa yadda taga dama.......gudaddun masu laifi daga kurkukun qasar Ethiopia masu tarin yawa.......masu muggan laifin da wasuma an rufe file dinsu da sunan sun mutu. Bakinta take son motsawa ta fadi abubuwa masu yawa da suke zuwa kanta a sannan,duk da ta sani wani binnannen abune da koda tafisu saninsa yayi nisa da tunaninta....... Cikin qanqanin lokaci ta sulale tayi relax sosai a jikin tafisu tana fita daga duniyar da muke ciki zuwa wata duniya ta daban. Yadda tayi a jikin tafisun ya bawa tafisu tsoro,lamari ne na matar maimartaba gaba daya. Ta tabbatar inda cikin hayyacinta mammina take ko jingina da jikinta ba zatayi ba duk da yadda tayi imanin tana amfanarta ne kawai,dole tsoro ya shigeta,ta kurma ihun kawo dauki,cikin sakannin da basufi qiftawar ido ba gurin ya samu daukin hadiman dake da ikn yin zirga zirga a rea din *A K H N A N* Ko kadan bataji wani abuba wai don ta dakatar da mammina daga gurinta ba,hasalima karatun da takeyi sai ya mantar da ita komai da kowa. Nannauyar ajiyar zuciya ta sauke sanda ta kammala littafin,ta lumshe idanunta a hankali tana rungume littafin a qirjinta. Ba abinda ke mata yawo akai sai dabi'un ma'aiki masu ban sha'awa da qayatarwa. Dabi'un sanyin hali,kawaici haquri tausayi kyauta da martabawa mutum koda bawa ne. A hankali ta koma kan mu'amalarsa da iyalinsa,bata taba karanta labarin madaukakin mutum wanda bai dauki kansa komai ba a gurin iyalinsa ba irin annabin rahama. Ta saki murmushi kadan sanda ta tuna inda ta karanta,nana aisha tabi sahunsa sanda ya zame jikinsa daga makwancinsa don zuwa ziyara maqabartar baqee'a(yakanje nemawa al'ummarsa da suka rasu sassauci),ta dauka zaije dakin daya daga cikin kishiyoyinta ne,sanda yake dawowa ta dawo da gudu gudu don ta rigashi isowa daki,ta koma ta kwanta luf,saidai yana kallonta da yanayin yadda qirjinta yake dagawa ya fahimci komai,yayi murmushi. Sake murmusawa itama tayi tana shafa lallausar sumar saman kanta da dankwalin yadan zame kadan. "Kishi?" Ta fada a hankali kamar tana tambayar kanta da kanta. Saita juya idanunta kadan,tana sake tambayar kanta......akan waye zataji irin wanna kishin?,ko akwai lokaci?,ko akwai wani da zata iya jin halittar kishi haka a kansa?. "Muhammad haisam ne" Kai tsaye taji zuciyarta ta jefa mata amsar. Guri daya ta zubawa ido,tana jin shakka akan hakan. Wanne matsayi ya taka a ranta da zuciyarta da zataji irin haka a kansa?,DABI'U ta yarda dabi'unsa nargartattu ne......musamman a yanzu data sake karanto daga inda yake koyinsu......suna masa kyau kuma.......ta yarda da haka,suna qara masa wata irin kamala.......amma shike nufin lallai zata soshi. "Allah ya taimakeki" Taji an fadi daga gefanta. A nutse ta daga idanunta tana duban birra dake rusune daga gefanta. "Inata magana......amma kin zurfafa a tunani.....ban taba ganin irin wannan zurfin tunanin daga gareki ba......Allah yasa lafiya" Idanu ta zubewa birra din,a tsakanin awannin nan......tsakanin awannin da komai ya wakana zuwa yanzu wasu irin sauye sauye take gani. Basarakiya ce ita.....wadda ta rayu cikin sarauta da mulki,tana iya karantar kowanne motsi hali da dabi'ar abinda ke kewaye da ita idan ya sauya. Da yawan hadiman dake mata tattaki yayin fita wani guri ko cikin gida idan ka debe su birra basu bane yanzu. Yaushe aka canzasu?,waye yayi canjin ba tare da masaniyarta ba batasan wannan ba. (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) "Yaushe kika koyi bin qwaqwqwafina?" Rusunawa birra tayi sosai. "Tuba nake.......kawai ina qoqarin kiyaye amanar da sheikh yabar mana ne". Shuru ta sakeyi,kamar kowanne lokaci idan birran ta fadi wani abu daya dangaceshi. Tafiyar kwana uku yace zaiyi......amma batasan ina zaije ba.....wa ya sani cikin qasarsu?. "Yaushe kika fara damuwa da abubuwan da basu shefaki ba?" Taji zuciyarta tana mata tambayar data sanya komai nata tsaiwa cak. Siririn tsaki taja......ya akayi take dulmiya kanta a hankali akan lamarinsa?. "Ki bawa barratu litattafan nan ta wuce dasu.......zamu qarasa sassan morsa safiyya" Ta furta tana jin ya kamata ta amsa kiran nata. *M O R S A S A F I Y Y A* Kusan komai ma da yake faruwa cikin gidan a yanzu ba damuwarta bane......kusan duk wani abu dake wanzuwa batajin yana cikin damuwarta. Damuwarta daya ce AKHNAN biftun safeena.......kuma ta tabbatar ta shiga hannun da koda ita daya ta rage a duniya ba zata wulaqanta ba muddin shine mijinta. Ta kammala komai.......idan akace komai ciki harda rabon lafiyayyen invitation din gayyatar bikin da ta tsara yi na kwana biyu kacal. Bikin da tayi wani irin gayyatar girma da ba wanda yasan plan dinta na hidimar. Kowa ma tanason masa ba zata ne,wani irin bikin na zallar gargajiya da al'ada wanda aka haura shekaru hamsim ba'ayi irinsa ba. Komai da komai cikin gidan ta tsara za'a yishi ba tare da an fita ko ina ba. Ta gama tanadarwa akhnan komai.......idan akace komai komai da uwa ke tanadarwa d'iyarta da zata aurar auren ma irin auren farko dinnan. Lokacin da suka tattauna da sultane kuma akan falaak,akan maleek dakeson a yarje masa auren falaak sai taji hawaye yana taruwa cikin idanunta. Wane irin karamci wannan daga ubangijinta?......irin karamcin da bata taba zato ko tunani ba?. Aminin sheikh haisam ta tabbata sheikh haisam dinne,banbancin da zai zama a tsakaninsu d'an qanqani ne. "Me zamu jira Allah ya taimakeka?.......me zai hana a daura auren ayi hidimar dukka lokaci daya?" Ta fada tana jin nutsuwa da gamsuwa har cikin ruhinta. Ko ba komai ta sani.....aminin haisam komai nasu zai iya zama daya kaman yadda qasarsu take daya.......kasancewar falaak tare da maleek zai zama tamkar kasancewar falaak din da akhnan ne. Wannan kadai zai sassauta zai kuma ragewa akhnan kewar gida......zai kuma sake bata daman tattara hankalinta gami da rage qiyayyar auren a ranta. Murmushi sultane ya saki yana jin wani farinciki shima......farincikin da ya tabbatar ya haura wanda morsa safiyya keji. "Da sauri haka safiyya?". Qasa tayi da kanta tana murmushi. " Ba domin ita ba......sai don jin dadin d'iyata.....saidon diyata taji cewa ba ita kadai bace tabar gida" Murmushi ya sake kubce masa,yana mamakin yadda a komai morsa safiyya ke fifita masalahar akhnan sama data kowa......koda kuwa d'iyan cikinta ne......anya akwai qanwar uwa a zamin nan irinta?. "Wato harda ke hairaan.......aka hadu aka yiwa diyata fashin miji.......sheikh ta gani takeso......amma kuka mata taron dangi kuka hadata da abokin sheikh?". Murmushi da yafi kama da dariya dukkansu sukayi,morsa safiyya na mamakin yadda yaji zancan. Duk da tasani,shi din aminin 'ya'yansa ne,mulki ko wani abu makamancinsa bai hanashi jan yaransa a jiki ba. "A duk sanda bawa yabar wani abu saboda girman zatin Allah.........a duk sanda wani bawa yabar wani abu saboda maslahar dan uwansa........saboda danuwansa ya samu.......to lallai Allah zai musanya masa da abinda yafi zama alkhairi" Kai sultane yake jinjinawa. Wannan hankali da nutsuwa ta hairaan ya sanya ko yaushe yake jin kamar daga jikinsa ta fito itama. "Haka yake.......munyi magana da Muhammad........kuma na samu gamsuwar shida maleek duk daya ne.......a ranar juma'ar nan,iyayen maleek zasu iso daga masarautar gera,inda mahaifin maleek ke sarautar yankin.......abokina bobbo muhammad dawud ya sake bani tabbaci a kansa......ranar juma'ar zai d'aurawa falaak aure da maleek......kwana shida suka rage kacal a yanzu......amma kuma.......inason suma saudiyya ya zamana guri na farko da zasu fara zuwa itama don su nemawa kansu da kansu albarkar aurensu.......zan bude ticket na sheikh da akhnan da qarin kwanaki daban......zan baki dama ki gudanar da bikinki don nasan kina da buqatar hakan......zan hada tafiyarsu tare kwana biyu da gama bikinki". Wasu irin hawaye morsa safiyya taji......wani hawaye me yawa da wani irin d'umi yana bin kuncinta. Ba zatace sultane baida wani alkhairi a tattare da ita ba......ba zatace sultane bai mata kowanne alkhairi ba iya zamansu.......amma dai wannan......wannan damar da wannan abun da yayi mata yana cikin manyan abubuwan da idan zata lissafa zasu kasance cikin sahu da list na gaba gaba. A ranta takejin dukkanin burikanta sun fara cika.........burikanta burikan safeena......tana jin kamar ta fara cikawa safeena wani sashe na burinta.......idan har ta kammala da wannan........ranta zai zama fansa ne gurin bankado inda AHMED da jaririn safeena na ajani suka bace......koda hakan shine zai zama fansa kuma sanadin ranta. *Akhnasaim tales*🤍 *zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 08187255862 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 08187255862 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 07* A yanzun da akhnan ke takowa zuwa babban parlor din daya zamana kusan a yanzu morsa ke yini saboda shiryen da suka zame mata linki biyu,na akhnan din dana falaak,falaak din da a gobe juma'a ne zai zamana cikar ranar daurin aurenta da maleek,sai akhnan din ke dubansu tun daga nesa ba tare da sunsan da shigowarta gurin ba. Cikin tsakiyar suke da wasu irin akwatina da ba zatace ga abinda yake ciki ba. Tarin Invitation da tana iya ganin qyallinsu daga inda take takowa,da wasu suturu a gefe da amintattun hadimanta ke ninkesu suna shiryasu. Ta maida dubanta kan hairaan da falaak,sai takejin kamar ita daya ce bare a cikinsu. Farinciki ne kwance saman fuskokinsu,hairaan din ta kaiwa falaak duka tana fadin. "Mara kunyar amarya kawai" Sai falaak ta saki dariya tana boye fuskarta. Ko alama bata taba kawowa zataso wani a kusa irin son da taji tana yiwa sheikh Muhammad haisam ba,amma daga randa ya zama mallakin bifttunta sai duka ya koma mata kamar bai taba tsugunnawa a wani gurbi na zuciyarta ba. Komai da morsa safiyya keyi ta saki tana tattara hankalinta akan akhnan. Fuskarta da wani kalan murmushi da taji wani abu ya tsarga mata a yau ta nuna mata gefanta. "Zauna a nan" Tana zama kuma dukka hadiman dake gurin suka zube suna gaidata da girmamawa. Amsawa daya tayi musu,kowacce ta ajiye aikin hannunta suka jera layi suka fice. "Barka da warhaka tanti" Falaak ta fadi da muryarta da tayi wani irin wasai kuma tarwai. Kai ya gyada a hankali "Barka" Ta amsa mata,saita maida idonta kan hairaan. "Barka da wannan lokaci". Abun ya yiwa kowa dadi,wani abu ne da falaak din bata taba yi ba tsakaninta da hairaan din ba. "Barka kade qanwata......momma mufa fita zamuyi mu baki guri" Hairaan din ta fada tana miqewa,daidai sanda anwaar ke shigowa parlor din. Akhnan yaketa kallo yana rungume da qatuwar ball dinsa. Tun rabar data bashi wasu chocolate manya shikenan bai manta fuskarta ba,duk da batace masa komai ba batayi magana dashi ba amma shi bai manta ba,saita saki murmushi ta miqa masa hannu,take ya tajo da saurinsa,ta kama hannun nasa tana zaunar dashi saman cinyarta. Kai morsa safiyya ta dauke tana jin wani farinciki yana ratsaya,zuciyarta ta karye kaman kuka zai kubce mata. Sannu a sannu dai Allah yanata jefa soyayyar yaran a zuciyarta,wanda tana da yaqinin zamowa sa zasu yi da falaak a qasa daya zai sake kawo kusanci a tsakaninsu,tunda dukkaninsu basu da kowa basu da wanda yakai junansu. "Zai bata miki fa wannan kyakkyawan farar doguwar rigar.....yaje sumayya tayi masa wanka" Kai ta girgizawa hairaan alamun ta barshi,saita daga idanunta take kuma suka hada ido da morsa safiyya alamun ita take kallo tun dazun. "Barka da yamma,kin yini lafiya?" Morsa safiyya ta fada kai tsaye sanda dakin ya dauki shuru bayan kowa ya fice ya barsu. Karo na farko.......lokaci na farko da taji wani nauyinta ya kamata. Karo na farko da taji kaman hakan bai dace ba..... Murmushi morsa din ta saki,boyayyen murmushi dake fassara farincikin da takeji,ta gama karantar me takeji,kunya da rashin sakewa......yau ita akhnan kejin kunya?,yau ita akhnan ke qin sakewa a gabanta don ita ta fara gaidata?. "Kada kiji wata kunyata......hakan ba mummunan abu bane.....uwa tana iya gaida diyarta ta kyakkyawan hanyar tambayar lafiyarta irin haka.......yanzu ba wannan ba....." Morsa ta fada tana jawo wani qaramin akwati. Sai data saka hannu ta dauke anwaar tana dubansa. "Kaje gurin sumayya ta karbi madara" Batama qarasa ba yayi jifa da ball din nasa yana nufar qofa,sai akhnan din ta bishi da kallo har ya bace kafin ta dawo da dubanta ga morsa. Saman cinyarta ta aza mata akwatin. "Ina me fatan sauke wannan nauyin da amanar dake wuyana shekara da shekaru....." Morsa ta fada muryarta tana rawa. Haka kawai tunda ta kalli akwatin taji ta dokanta ta budeta,bawai don kyanta ba,aah hasalima kana kallonta kasan tsohuwar akwati ce. Ta danyi kiciniya kadan da ita sannan ta gano gurin budeta ta bude,don daga maganan farko morsa safiyya bata iya sake cewa komai ba,hasalima hawaye take daukewa a dabarance da tissue din hannunta. (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) Bracelet ne na danyan gold......(dan uwan wannan bracelet din dake hannun mammina da haisam ya sauya mata da fake dinsa). Abun wuya da dan kunnaye da sauran kayan tarkacen kwalliya na gold data tabbatar na mahaifiyarta ne,don koda ba'a gaya mata ba tasan tsohon gold ne don dukka tsaffin design aka masa. Haka ta dinga fita dasu daga qarshe kuma taci karo da wata takarda da littafi. Littafi ne na addu'o me shafuka kusan hamsin,wanda aka rubuta da yaruka uku,oromo da yaren Tuareg wato yarensu na buzaye sai yaren larabci da shine asalin rubutun. Ta sauka zuwa ga mawallafin sai sunan safeena din baro baro ya bayyana. Mamaki ya sanyata daga kai kadan ta kalli morsa safiyya,alamun tambayoyine fal cikin idanunta. "Mahaifiyarki macace me Tarin ilimin addini.....ilimin addinin daya zame mata jagora gurin karbar dukka qaddarar rayuwarta.......wannan littafin shine abu na qarshe data wallafa sanda ya rage mata kwana casa'in kacal tabar duniya". Wani nauyi ya sauka a zuciyar akhnan,ta aza idanunta akan takardar dake da gajeran rubutu cikin yaren Tuareg. _Wadannan sune kadai abinda na mallaka yake 'yata,kuma sune abinda nabar miki,ina fata su isa gareka sanda kike shirin tafiya dakin mijinki.......ZAMANKI MACE TA GARI SHINE CIKAR BURIN RUHINA da salamar gangar jikina_. Damqe takardun tayi a hannunta tanajin hawaye yanason taruwa cikin idanunta. "Alfarma nakeso kiyimin......ki kafa tarihin zama kusa da safiyya......ki kafa tarihin kin rayu cikin gidan safiyya koda na iya kwanakin nan ne......inason ki qarasa kwanakin a nan sashe na cikin 'yan uwanki,hairaan da falaak da zata amsa sunan matar aure juma'ar nan itama......wannan ta zama alfarma guda daya da zan dinga tunawa da cewa kinyimin ita a rayuwarki". Idanunta dukka ta bude a hankali tana duban morsa safiyya,idanunta da a yau sai take ganin suna hango wani abu daban da dukka shekarun baya bata taba ganinsu a fuska da idanun morsa safiyya din ba. Ta yaya ma zata iya cewa a'ah.....matar data sake kusantata da wani abu daya shafi mahaifiyarta?. ★★★ "Bansan wacce irin sa'a ce dakai ba har da mukayi nasarar samun hayyacinta ka tatsi dukka wadannan bayanan daga gareta ba" Dr na'eem ya fadi yana share gumin goshinsa da qaramin lallausan handkerchief na towel din dake hannunsa. Kujera yaja ya zauna,ya sake daga idanunsa yana duban haisam dake tsaye qiqam gaban gadon da yalwa ke kwance akai kamar sojan da aka bugawa kugen yaqi. Gadon da a dazu ya dinga jijjiga da jijjigar da gangar jikin yalwa keyi. "Sun riga sun ciyar da ita wani abu da zai dinga kashe mata organs dinta,kowacce rana zatayita mutuwa ne ba tare da tasan mutuwa takeyi ba.......idan da ta dauki wani lokaci a haka,za'a je ne kawai a tsinci gawarta ba tare da ansan meye yayi ajalinta ba" Dr na'eem ya qarasa bayanin yana bude gorar ruwa yakai bakinsa. Da wannan nutsuwar tasa dai ya sauke dukka hannuwansa biyu qasa. Da wannan nutsuwar tasa yayi tattaki ya jawo kujera ya zauna,da wannan zaman nasa dake nuna izzar mulkinsa. A dukka bayanan daya qarqare samunsu......ya fahimci wasan da mammina tayi da hankula masu tarin yawa.....ciki kuwa harda hankulansu yalwa din. A iya saninsu da abinda suke iya gani,a iya mu'amalar da takeyi dasu suna zaton sune na gaba gaba abokan sirrinta,tunda sune sukafi kusanci da ita,saidai wani abu da basu sani ba......wadannan wulaqantattun bayin......wadannan hadiman da ko kusa da ita basu isa suzo ba sune mafi kusanci da ita. Ya gane hakanne bayan ya qwamushe mutumin dake kula da duk wani kwandunan shara na sassan nata,ya wankesu bayan an yasar da sharar,ya kuma maidasu muhallinsu. Miqewa dr na'eem yayi,suka bawa juna hannu shida haisam kafin su rankaya tare da haisam din su fice suna sake tattaunawa. Tafiya me dan tazara sukayi kafin su kawo ainihin muhallin ajiyar motoci inda Dr na'eem yayi parking motarsa,ya bude ya shiga sukayi sallama,sannan shima yayi taku biyu baya yana duba agogon hannunsa. Juma'a ce......juma'ar daya kamata ace yana masallacin masarauta......ya samu jam'i kamar yadda ya saba. Juma'ar ita ya tsara zai koma masarauta.....juma'ar a ita ya lissafa aikinsa ya kammala. Eh aikinsa ya kammala.....saidai yanason budewa mammina qofa daya tal cikin tarin dubban qofofinta daya bude kowacce ya zare maqullin kuma ya yasar........don haka yana buqayar ranar LAHADI. A ranar lahadin ta sace Ahmad din ta rabashi da tsatsonsa ta kuma batar dashi......a wannan ranar.....a daidai lokacin yakeso ya maido mata da saqonta. "Zamu iya tafiya?" Salana ya tambayi haisam cikin girmamawa. Dauke idanunsa yayi daga kan agogon,bayan ya duba lokaci harda kwanan wata ya duba yana lissafin watannin daya share a agadez......yana lissafa watannin daya diba baiga nanay dinsa ba. Yana kewarta.....yana tsananin kewarta sosai,wannan aikin na kwanakin nan daya sakashi a gaba ma ya sanya ko waya basuyi ba kwata kwata,saidai time to time yana ganin saqonnin noorah rumaisa da Anaani,musamman noorah dimma,kamar ita da taufeeq sunfi damuwa da nisan da yayi dasu,duk da yasan kowa a cikinsu ma hakan ya keji,sun fisu dauriyar boyewa ne kawai. "Su khadeem fa?" Ya tambayi salana a nutse. "Yau daurin aure,dukkaninsu suna cikin agadez......sunce na barka ka kammala uzurinka". "Ya salam" Ya furta yana nutsa yatsunsa cikin sassalkan gashinsa. Bai taba hango daurin auren maleek ba babu shi a gurin......bai taba hango maleek zaiyi aure bai halacci daurin auren ba. Wayarsa ya soma laluba,me yasa zasu masa haka?,suce kada a tuna masa?. Duk yadda aikin yake da muhimmanci nasu muhimmancin na dabanne,bayajin akwai wani abu da zai shiga cikin wannan alaqar......ya kuma tabbatar kowa da kowa cikin team 7 din yaje banda shi. Bai kira maleek kai tsaye ba,don bayason raba masa hankali a irin yanayin nan daya tabbatar zumudi ne fal cikin maleek,sai ya kira omar *Akhnasaim tales*🤍 *zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 08187255862 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 08187255862 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 8* ,kiran da yana shiga bugu uku kawai omar ya daga. "Me yasa haka omar?" Yayi tambayar cikin sanyi da nutsuwarsa,saidai akwai yanayin da zai nuna maka qorafi yakeyi. "Noooo captain......you're forgiven fa,dukka nauyin Ethiopia ne a wuyanka......and you need to stay at home......kowa yazo,hakan kuma yana nufin zuwanka gurin baiyi daidai ba,cikin wadanda sukazo din ba kowa bane yasan kana nan ba........dole sai ranar daya kamata ka fita din.......sallah kawai zamuyi yanzun a daurawa wannan angon mara kunya auren nan muma mu huta......sceret mana sir" Murmushi kadan ya saki a boye,ya yadda da maganan omar,dole ya zauna a gidan gudun ballewar wani liqi daga mutanen da sukazo.....amma dai maleek dama sauran duka nashi ne. "Alright......." "Akwai wani walima da sukeyi idan an gama daura auren duka maza da mata......inajin harda Madame dinka ma" Shuru ya gilma kadan,kafin haisam yadan waro idanunsa. Kaman zaice wani abu amma sai ya fasa. "Alright" Ya sake fadi yana katse kiran saboda jin muryar naseeb yana kiran omar din. Wayar ya ajiye a hankali yana sauke ajiyar zuciya. "Walima?.....maza da mata" Maganan yadan sake dawo masa akai,sai ya sake daukan wayar ya soma lalubar number abdii. Har kiran ya shiga,sai kuma ya soma tambayar kansa me zaice masa?. Me zaice masa shine dalilin kiran?,bai bawa kansa amsa ba yaji muryar abdii ya daga kiran. "Barka da juma'a obbo" Ya furta cikin girmamawa da kuma wani nishadi cikin muryarsa. "Yauwa abdii.......fatan komai lafiya" "Lafiya alhamdulillah obbo......yau obbo maleek zai angwance" "Ba shine aikin dana baka ba" "Obbo ina aikina.....komai lafiya yake obbo" Shuru haisam din ya danyi,kamar meson tambayar wani abu ko kuma tuhumar abdii akan abinda baisan meyeshi ba. "Yayi.....ka sake kula sosai" "In sha Allah obbo" Katse wayar yayi a gefe,ya tattara hankalinsa kan titi da suke wucewa da nutsatsen tuqin salaana,salon tuqin daya sanya ya zabeshi cikin kaf drivers dinsa,yakan zabi kuma ya tafi dashi ko ina ne. Sanda suka isa gida ya duba lokaci sai yaga akwai sauran lokaci na tafiya masallaci. Yayi zaune a motar,yana duban wayarsa kamar meson tuna wani abu daya manta. Sake daukan wayar yayi ya budeta yana lalubar sunan nanay dinsa. Daidai lokacin da nanay din ke zaune ita da Khansaa tana duba list din komai da aka zuba cikin gidan narkakken ginin gidan haisam. Khansaa da tafi kusa da wayar ita ta miqa hannu ta dauki wayar,ta saki qaramin murmushi ganin sunan dake rubuce. Amini kuma abokin shawara qaninta haisam,duk kuwa da cewa ta girme mishi,amma ta bashi dukkan girman da komai ma. Kallon wani babban yaaya ko kuma uba take masa,yana kan dukkan damuwarsu da matsalarsu da shawarwari dama dukan abinda ya dace ace yayi. "Obbo ne" Tace da nanay tana dariya,sannan kai tsaye ta daga wayar tana sakata a kunnenta. "Assalamu alaikum......i missed you" Ya fada yana jin rauninsa yana dawowa. Indai a gaban nanay ne.....indai nanay tana nan to yana jinsa shi ba komai bane.....shi ba kowa bane.....yana jinsa ne tamkar d'an jariri. Duk wani power tarin tawaga.....manyan ayyuka masu munin hatsari da yake aiwatarwa a gaban nanay yana jinsa kamar ba shi ba.....kamar ba wannan Al_saamit din ba.....the silent one. "Dan nanay.....ba nanay din bace" Khansaa ta fada tana murmushi mai sauti. Fuskarsa ta saki kadan,ya dora hannunsa saman sumarsa me santsi yana shafawa a nutse idanunsa suka lumshe sannan suka bude duka lokaci guda. "Oum maheer" Ya furta a nutse. "Captain obbo.....munyi kewarka,kowa ya shirya.....dukka masarauta kai ake jira,surukarmu mukeson gani,duk shirye shirye suna dab da kammala" Ta fadi cikin zumudi gami da son ganin matar captain sheikh din. Murmushi mara sauti ya sakeyi,da girma haka suka dauki lamarin?. "Sati uku captain kamar yayi nisa" "Kubi komai a hankali obbolettii(sister)" Ido ta juya kadan tana duban nanay. Ba su kadai ba,daidai da nanay din tasan yadda ta dauki abun kadai bazai sanya kowa ya zauna ya nutsu ba har sai sunga isowarsu. "Karka damu qanina......kaidai kawa kayi qoqari ku iso da wuri" "In sha Allah" Ya amsa mata sannan ta miqawa nanay. Cikin muryoyinsu yakejin wani irin shauqin abun,cikin muryoyinsu kadai yana iyajin dokin auren da kuma son iswarsu Ethiopia. Ya sake shuru bayan sun gama wayar dasu. Har yanzu yana jin wani emptiness da baisan daga inda yake ba,irin yanayin nan da mutum yakejin kamar akwai wani abu daya kamata kayishi amma ka rasa meneshi. Siririyar ajiyar zuciya ya sauke,sannan ya kwashi wayoyinsa kawai,ya zura qafafunsa a nutse yana fita a motar. Cikin gidan ya shige kansa tsaye,yau sai yaji gidan ya masa shuru da yawa. Cook dinsa ya soma tambayarsa me yake buqatar a zuba masa. "Black tea da dabino" Shi din kawai ya karba yasha yana hadawa da dabinon ajwa da yasan shine dabinon haisam din,duk da yana cinsu kala kala amma yafi mu'amala da ajwa din. Wanka ya shiga yayi,ya kuma shirya tsaf cikin Moroccan thobe olive green data masa wani irin sassanyan kyau. Wayarsa ya sake dauka yana dube dube,shi kansa baisan dube duben me yakeyi ba,sai yaja dan siririn tsaki ya sakasu a flight mode duka biyun,ya dauki abun sallah ya zura lausasan flip flops a qafarsa masu sauqi ya feshe jikinsa da wannan lallausan turaren nasa sannan ya doshi qofar fita. Akwai masallacin juma'a daya gani gaban anguwarsu kadan,basu da wani nisa,sai ya yanke zuwa can din yayi tattaki da qafa ya samu juma'arsa a can. Sanda aka kammala juma'ar sai yayi zamansa cikin masallacin. Lokacin sai ya zame masa wani dan taqaitaccen lokaci na samu nutsuwa da kebe kai daga mutanen da suka sanshi. Emptiness din da yakeji yayi yawa,don haka ya dauki qur'ani cikin drawers na masallacin da aka adana ya soma tilawa da wannan sautin qira'ar tasa me matuqar jan hankali da sanya nutsuwa. Awa daya kawai yayi ya rufe,ya miqe a hankali yana maida qur'anin sai ya fahimci akwai idanuwa sosai dake satar kallonsa a masallacin. Inde irin wannan kallon ne ya saba dashi,ballantana a yanzun da ya tabbatar yayi daban da qabilar da yake rayuwa a cikinsu,so dole ya samu wannan qalubalen. A nutse yake takawa zuwa gida,saidai still yana jin wannan yanayin. Ya furzar da iska daga bakinsa a hankali maganan abdii tana dawo masa. "Walima zaayi maza da mata.....bayan gama daurin auren" Hakan na nufin kowa ma zai fito.....kowa ma zai halatta. "Amma ita fa?" Ya tambayi kansa. Shuru ya gilma ta cikin kansa,ba wani amsa ko motsi daya dawo masa da sunan amsa,sai kawai ya samu kansa da sauya akalar tafiyarsa zuwa gida. *A G A D E Z P A L A C E* Cike masarautar take a wannan juma'ar da ninkin jama'a baqi da 'yan gari da suka saba zuwa sallah babban masallacin juma'ar na gidan sarkin. Cikar yau ta banbanta data kullum,saboda gudanar da d'aurin auren falaak sultane muhammad hammud da kuma maleek motii ja'afar. Wata irin qauna da soyayya mutanen yankin agadez suke nunawa sultane din,wanda adalcinsa da soyayyarsa ga jama'arsa duka ya siya masa wannan. A qurataccen lokaci aka sanar da daurin auren......amma adadin jama'ar da suka halatta zaka dauka abu ne da aka jima ana shelar daurashi. Masarautar ta cika da baqi...ko ina kai kawon al'umma ne da kuma hidimomi da zasu tabbatar maka babban sha'ani ne ya samu masarautar. Tsaye take gaban babban mirror din dake girke cikin dakin daya zama mallakinta tun sanda ta dawo da kwana sassan morsa safiyya. Wani irin daki ne dake da wani irin tsari da kyau me daukan hankali,dakin da bata taba zaton akwai me yanayinsa cikin gidan ba. Ba wannan bane.....abinda yafi daukan hankalinta da kuma sanyata yawaita zubawa morsa safiyya idanu a duk sanda ta shigo gurinta shine. Tasan komai da tafi buqata cikin dakin baccinta.......tasan kowanne tsari nata.....tasan komai da yake qayatar da ita yake kuma burgeta,tun daga kan color na dakin da duka tarkacen furniture da aka zuba cikin tsari da burgewa. (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) Akwai wani yanayi me dadi da dakin yake dashi.......yanayin kuma daya hada da sassanyan qamshin turarukan da kowanne rana ake cudesu dashi ita da falaak din,duk da falaak din tana nata dakin daban,amma komai iri daya,komai tare momma take musu. Wasu irin turaruka ne daga asalin gargajiya. Turarukan nan dai na kamfanin *INCENSE BY KABO DAUGHTER 803 211 9803* Wani irin mayen qamshi da hatta da numfashin dake fita a daga hancinsu da hucin qamshin yake fita. Baya barin sutura da gangar jiki da wuri,sannan a sake dora musu wani. Saidai duk da haka.....duk da nutsuwa da dadin da wannan qamshin yake mata......duk da irin yadda qamshin ya mata dari bisa dari......har yanzu dai. Har yanzu akwai wani qamshi guda daya da tayi kewarsa.......tana jin akwai wani qamshi qwalli daya da kamar ta rasashi a dukka tarin qamshe qamshen dake zagaye da ita. Ko yanzun da take tsaye gaban madubin.....a shirye cikin wata irin doguwar riga ta alfarma da aka saqata daga qasar dubai......wani qamshin ne a jikinta na musamman yake tashi,amma kuma tana jin akwai sauran wani gurbi daban......kamar akwai abinda take jiran samu......kamar akwai abinda take jira taji. Ta soma zargin kanta sanda lasifiqar babban masallacin ta fara motsawa,muryar na'ibi ta fara tashi yana tayar da iqama,sai ta samu kanta da tattara dukka hankalinta akan kowanne furuci na iqamar da yakeyi,ta miqa hannu ta jawo stool ta ajiye gaban mirror din,ta kuma zauna akai a hankali zuciyarta tana bugawa kadan kadan da wani irin yanayi da batasan me ya kawoshi ba. Idanunta zube saman fuskarta tana duban kanta da kanta. Taga irin kyan da tayi ita kanta,....taga yadda fatarta ta sauya daga ainihin fatarta data sani zuwa wata lafiyayyar fata da ita kanta burgeta takeyi. Ita kanta burge kanta takeyi,to amma duk da haka a daidai wannan lokacin sauraren da kunnuwanta sukeyi sunfi ganin kyan jikinta dana kwalliyarta muhimmanci. "Allahu akhbar......bismillahir rahmanir raheem......alhamdulillahi rabbil Aalameen....." Muryar limamin dake jan sallah a daidai wannan lokacin ta shiga cikin kunnuwanta. Idanunta ta mayar ta lumshesu a hankali,tana ci gaba da sauraren karatun sallar juma'ar amma kuma wani abu yana mata nauyi yana danne zuciyarta. Kamar wata murya ta daban take buqatar ji ba wannan ba......kamar wata murya daban tayi tsamamanin ji ba wannan muryar da ake karatu da ita yanzu ba. "Yau.....Kwana hudu kenan" Ta fadi can qasan zuciyarta,sai kuma ta ware idanunta da dan sauri "Me yasa nake irgawa?me yasa na irga?" Ta samu kanta da tuhumar kanta da kanta. Miqewa tayi a hankali tanason watsar da komai,kunnuwanta suna iya jiye mata saututtuka kala kala,wanda kusan fin rabinsu na karadin falaak ne da qawayenta da kusan duka cousins dinsu ne. Ajiyar zuciya ta sauke,daidai sanda aka turo qofar dakin,saita waiwaya a nutse don ganin wanda yake shigowa. Morsa safiyya ce......morsa safiyyan da a yau tayi mata wani zuzzurfan kallo.....zuzzurfan kallon daya nuna wasu kamanni nata da na safeena. Kamannin da ita ta sansu ne kawai ta hoto,hoton da ta hannun morsa safiyya,ta silar morsa safiyya kadai ta mallakeshi,sai taji zuciyarta ta mata nauyi,wani abu me kama da nauyin maraici yanason ya saukar mata,amma kaman safiyyan ta fahimci haka saita qaraso gabanta,ta kamo kafadarta tana rungumeta cikik jikinta. "Alhamdulillahi......Alhamdulillahi" Ta maimaita har sau uku,sautin muryarta yana yiwa akhnan zurfi tana jin a yau kamar muryar safeena ce cikin tata,muryar data mallaketa ta wannan tsohon cassette din recording din,cassette din daya zame mata abokin hira takan maimaitashi a rana sau babu adadi. Rungumar da momma din tayi mata saita dinga ji kamar ana sauke mata wani abu......sai taji kaman wannan damuwar data mata yawa tana raguwa. Saitaji wani irin sassauci yana saukar mata a hankali. Wani yanayi da bata taba jin irinsa ba ballantana makamancinsa. *zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 08187255862 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 08187255862 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 9* "Ubangiji ya tsareminku daga dukkan sharri,ya tsare gabanku da bayanku......kiyi sallah,zan turo birra ki fito farfajiya kema cikin ahalin safeena,cikin jinin safeena 'ya'yan 'yan uwanta,wanda na tabbatar inda tana Raye a yanzu abinda zatayi kenan. Zama cikinsu.....taji ta kalli taron daurin auren 'yar uwarki falaak" Ta qarashe maganan da wani rauni tana zame hannunta daga nan akhnan. Idanun akhnan akan morsa safiyya din,tana sake jin wani yanayi me kama da karyewar zuciya. Taci gaba da kallon morsa safiyya dake mata murmushi har xuwa sanda ta juya tana fita a dakin. A sanyaye ta wuce shiyyar da take salla a dakin,ta dauki after dress da yalwataccen mayafin dake ajiye a gurin saboda sallar,ta dora a kanta ta kabbara sallar. Tana sallamewa birra ta shigo,saita taimaka mata ta fidda after dress din da mayanin,ta gyara mata zaman gown din jikinta komai ta maida mata muhallinta,sannan ta take mata baya dauke da wayoyinta. 'Yar farfajiya ce dake tarwai da haske. Ba hadin rana da zuwa gurin saboda wadatar wasu irin shuke shuke masu daukan hankali a gurin. Komai na sassan morsa safiyya sai taga yayi daidai da tsarinta da ra'ayinta,bata kuma san dalili ba. Tsahon shekarun......wannan shine karon farko data fara sanin gurare da sasanni dake bangarenta,wanda ba daya data sani banda parlour dinta da take shiga a duk sanda aka tilasta mata zuwa gaidata. 'Yammata ne zaune saman wasu lausasan kilisai saqar qasar turkiyya masu tsananin kyau da daukan hankali. Duka kusan cousins dinta ne,sa'anninta da sa'annin falaak,dukka sun saje saboda tazarar shekarun duka uku ne. Fitowarta gurin ta aza mamaki a zukatan kusan dukka wanda yake gurin,har ta ankara da haka ta soma jinta kamar cikin wani baqo ko sabon guri. Mamaki kusan suke na fitowarta cikinsu,saidai yadda kowa ke qoqarin karbarta da ja a jiki ya bata sakewa kadan,ta kuma taka zuwa shiyyar da kakanni da iyayen safeena suke zaune suma ta zauna cikinsu. Shehnaz ce ta tako itama cikin kyakkyawar shigar shadda da aka yiwa dinkin mali ta zauna gefanta. "Bansan ina momma takeso kikai wannan kyan ba......karku susuta sheikh fa........kar kisa karatun nan yayi nasa guri". Karon farko magana irin wannan ta sauka saman zuciyarta ta zauna daidai. A hankali sai zuciyarta ta tafi wani tunani na daban,haka kawai ta samu kanta da lumshe idanunta tana jin wani abu ya harba cikin jikinta. Ganin bata amsawa shehnaz din ba,itama sai tabar batun ta maida hankalinta akan nanny dake magana da ita tana gaya.mata yau da dare me jan lallen aure zata shigo gidan har sai ta kammala da dukka amaren. Ba ita kadai ba,kusan duk wanda ke gurin dama cikin masarautar yana iya jin yadda aka fara siga ta daurin auren falaak a hankali ta daga idanunta a karo na ba adadi tana duban falaak din. Tunda ta shigo gurin ta fahimci wani kwantaccen farinciki a fuskarta.....tunda ta shigo gurin ta karanci sam ta kasa zama guri daya,ko ba'a gaya maka ba kasan cikin farinciki take wanda bata taba irinsa ba cikin rayuwarta. "Amma kuma.....me ya banbanta ni da ita?" Ta tambayi kanta tana tuna nata yanayin a dukka daurikan aurenta guda biyu da aka taba yi mata. Kuka baqinciki tashin hankali da bacin rai. Bata aminiya ba qawaye idan ka dauke aisa da shehnaz......daga aisan kuma har shehnaz banbancin ra'ayi da fahimta ne ko yaushe a tsakaninsu. Ba kasafai suke fahimtar nata ra'ayin da muhimmancinsa ba. Lokacin da waliyyin falaak ke shaida cewa ya bada aurenta ga maleek din.....lokacin ta aza idanunta a shiyyarsu. Wani irin qudundunewa taga tayi,tana wani dariya dake bayyana kunya da zallar farincikinta. Qawayenta nata zolayarta,hayaniyar gurin tadan qaru,don ma da alama suna ragewa ne saboda idanun manya dake gurin. Idanunta ta zare a hankali tana sauke ajiyar zuciya. MENE A CIKIN AUREN?,ta tambayi kanta da kanta,quruciya ke damun falaak din?,har take zaton wani abune babba na jin dadi cikin aure take masa murna haka?. Ko kuma ita dince?,itace bata fahimci komai ba?. Kai ta girgixa a hankali da yanayin da ba wanda zai gane,tafi zaton quruciyarce......tafi kyautata zaton rashin sanin ciwon kaine. "Auren soyayya dadi.....kaga ikon Allah yarinya zata rigamu shigewa ciki?" Shehnaz ta fada tana kama hab'a gami da duban yadda falaak keta sunne kai da alama dadi ne yake addabarta. Akhnan naji tayi shuru,bata kuma ce komai ba,malamar nan kuma da morsa ta dauko da niyyar mata training ta iso gurin,wanda wannan shine abinda ya tattara hankulan kowa a kanta. Ba wanda yasan dalilin zuwanta sai data zauna yiwa amare lecture. Tun akhnan naqin bawa maganganunta hankali har wasu daga ciki suka fara shiga kunnuwanta,bata kuma san me yaja hankalinta kacokam zuwa ga malamar ba tunani da hankalin nata suka daina rarrabuwa gurare. *_K'ARFE TARA NA DARE(A wannan ranar_* Sanye yake cikin emarati thobe baqa wul me sheqi da daukan idanu,wadda tana cikin sample na sabbin jallabiyyar da kamfaninsu dake dubai zai fidda a shekara me zuwa,sukayi masa tasa suka bashi kaman yadda aka saba. Cloak thobe ce a saman emarati din,wadda ta kasance gray color kalan zaren da aka yiwa emarati din ado dashi. Amama ne saman kanshi daya dace da cloak thobe din jikinsa,ya kuma haska wannan zagayayyar fuskar tasa ma'abociyar kyawawan labba,labban nasa da suka sake bada wani yanayi me kyau sakamon zazzafan black tea din dake cakude da qamshin coffee din da qasarsa take nomawa(Ethiopian oromian coffe da aka nomashi daga yankin jimma. Tsaye yake cikin sassanyan yanayinsan nan,yayin da khadeem dake zaune cikin da'irar abokansu ke qare masa kallo a nutse. Tunda yake bai taba ganin mutumin da wannan shigar kewa kyau irin haisam din ba. A duk sanda ya kalleshi sai yaga kaman saboda shi aka halicci shigar,a kuma duk lokacin da zai kalleshin limaman harami yake tuna masa irinsu sheikh yasir rashid addusary dasu abdurrahmanis sudais. Hira kawai ke tashi a parlor din da yaren oromo,sai turanci jifa jifa don bai daga cikin tilashinsu a yaruka. A farinciki suke dukkansu,kuma maleek ya hana kowa sakat kaman ba dare ne yakeyi ba. (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) Qamshin turarukansu masu aji ne cakude da parlor din,da sassanyan freshener din data zama tilas ga duk wani muhalli da zai rayu koda na qayyadaddun awanni ne,amma shigowarsa da tsaiwarsa a parlor din yana shan black tea din sai qamshinsa ya rinjayi kowanne qamshi dake parlor din da wani lallausan yanayi. Wayar abdii ce a hannunsa na hagu,yana viewing pictures din cikin wayar daya bayan daya,wanda duka wadanda akayisu ne dazu harda family din falaak a ciki sosai. Har xai ajiye wayar ya sake tafiya next picture,sai ya tsaya cak akan hoton yana dubansa. Daga baya ta fito ba daga cikin hoton ba,hasalima alamu dukka sun nuna batasan an dauki hoton ba,don fuskarta bata fita sosai ba. Haka kawai yaji wani abu yana sauka tsakani yatsunsa da tafukan hannunsa dana qafarsa. Sai.ya zame cup din da yakai bakinsa a hankali ya azashi saman table din da yake kusa dashi sosai. Yatsunsa ya sanya yayi zooming hoton,take fuskarta tayi kusa dashi sosai fiye da dazu,sai yayi clicking fuskar wyaar har sau biyu yana maida hoton anihin girmansa. A nutse ya daga wannan zagayayyun manyan idanun nasa ya zubesu akan maleek. "Maleek?" Ya kirashi da tone din daya sanya kowa a cikinsu ya maida hankalinsa kanshi. Wayar abdii ya daga masa,har yanzu idanunsa suna cikin nasa. Qanqance idanu maleek yayi,yanason ganin me haisam yake nuna masa. Ya gane hakan sai ya sake karkatar da wayar saitin fuskarsa shi kadai yana sake tsuke fuskarsa,bayan ya saka yatsansa daya yayi clicking sau biyu hoto yayi zooming. Second uku kawai ya bawa maleek dim ya dauke fuskar wayar daga idanun maleek din. "Matarka ba haja bace a kasuwa da zaka bada daman daukan hoto da ita......koda hoton mene bana tarihi ba.....ka kiyaye hakan" Ya fada da wani irin izza wani abu yana tasiri tun daga zuciyarsa zuwa saman fuskarsa. "Goge" Yace da abdii yana cilla masa wayar. Yadda ya cilla wayar banda abdii din ya nuna zafin naman cafeta ba abinda zai hanata faduwa ta fashe a qasa. "Amma......" Abdii ya bude baki zai magana,yanason gaya masa hoton tarihine,kuma ba kowa bane ya fito a ciki,yanason ya ganar dashi ba komai a cikin irin wanna hoton,amma kallo daya.....kallo daya daga haisam din ya kulle bakin abdii. "Tashin hankali" Omar ya fada qasa qasa yanayi sosa sumar kansa. Irin wannan kallon na haisam dukkaninsu sun sanshi. Kallo ne dake daureka da dukka wata jijiya ta jikinka,ya hanaka musu ko motsi har sai kayi abinda yace maka. "Obbo na goge" "Ka gogeshi daga trash ma" Ya fadi yana isa bakin fridge ya fidda ruwa mara sanyi ya soma zubawa a glass cup. *zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 08187255862 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 08187255862 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 10* Kallon kallo aka fara yi tsakaninsi,banda naseeb daya fuske. Har cikin zuciyarsa baiga laifin haisam ba.....ballantana haisam din da tun da can sunsan halinsa. Sarai ba wanda ban sanshi ba akan kishi,diya mace kadai wadda bai hada alaqar komai da ita ba kishinta yake ballantana wannan da igiyar aure ta gilma tsakaninsu koda ba soyayya?. Mutumin da kishinsa ya hanashi yayi soyayya da kowacce mace?. Saboda bazai so ba kuma sannna ya sakarwa wani?. Shi a karan kansa kallon haisam yake da yake fadin auren Akhnan tsani ne kawai zai zame masa.......amma ya sani,wani aure ne da Allah kadai yasan yaushe zai qare.......ga alamu nan kuma shi da kansa yana barwa kansa da kansa ba tare ma da yasan me yake aikatawa ba. "Da alama hoton dai yana da muhimmanci sosai". Khadeem ya fadi wanda idan bai tsokani haisam ba tun da can dama shi baya jin dadi. Ya jishi sarai,ya kuma fahimci inda ya dosa,amma sai yayi banza dashi,bai bashi amsa ba har sai da yayi bismillah ya dansha ruwan ya ajiye cup din. "Ba kowane ya kamata ya riqe wasu abubuwa ba" "Bafa hoton bane.....itace" Omar yayi gulmar da amjad da yafi kusa dashi,amjad din da mamakin haisam duka ya kasheshi ya kasa magana. Sam omar ya manta dabi'arsa......wani irin kaifin ji gareshi,bai kuma san haisam din yaji ba sai sanda ya bashi amsa sanda yake dab da fita. "Ban saba raba abinda na mallaka ba da kowa......komai da yake mallakata zai zauna a iyakokina har sai sanda ya daina amsa wannan sunan". Yana jinsu.....yana jin kakacinsu da komai nasu,ya tabbatar idan da yana zaune a cikinsu sai sun kusa cinyeshi,tsiya kam ya barsu a yanzu suyi son ransu. Murmushi kadan ya subuce masa,murmushin dashi kansa baisan daga ina ya taso ba.......kawai ya tuna yadda ya nuna ne. Shi kansa bazaice ga abinda ya jashi ba,bazaice ga abinda ya sanyashi yayi wani reaction din ba,abu daya kawai ya sani,bai samu salama har sai daya samu tabbacin abdii ya goge,duk da baida zargi ko haufi akan abdii din. "Me kenan?,kishi?....." Yaji tambayar ta subuce masa. Kansa ya girgiza a hankali yana dogare gwiwar hannunsa jikin murfin motor din. "Ba kishi bane wannan.....dom ba irin wanna feeling din na saba ji ba....." "Eh qarfin wannan ya d'ara na kishin da kake zaton kana dashi?.....saboda wannan din zahiri ne ba gaibu ba". Kai ya sake kadawa a hankali,ya aza dukkan qarfinsa yana ture tunanin gefe,don yana ganin maganan wani qofa daban da babu ita takeson bude masa,sai ya fidda wayarsa ya turawa omar gajeran saqo. _Zan shiga gurin sultane_ ya aike masa yana maida dubansa kan titunan da suke wucewa. _Ka sanar dani idan akwai buqatarmu a kusa,zan zama cikin shiri kusa da wayata_ Amsa ta shigo masa da gaggawa daga omar. Murmushi ya saki dan siriri,wanda har ya sanya har kyawawan labbansa suka bude kadan. Masoyin gaskiya ba qarya bane,ubangiji yana iya hada zukata suso junansu da tsaftatacciyar soyayya da aminci. Kaman dai......su bakwai din tamkar uwarsu daya ubansu daya,ba wanda keson ganin kuka ko damuwar daya,hakanan dukka team dinsa da yayi aiki dasu,da wani abu ya sameshi har abada suna zabar su ya samesu. Idonsa ya lumshe sannan ya bude,baisan yadda sultane zai karbi maganar ba..... Zai iya jurewa?......ko kuma bazai iya dauka ba?. Ya fidda numfashi a hankali yana tuna maganganunsa dazu da almaz. "Ka bari muje tare,na bayyanawa duniya na santa,nasan adadin fuskokin da take dasu......ta batamin hotona a fuskokin al'umma.........ta yaya sultane hankalinsa zai fara daukan ni d'ansa ne bayan na amsa sunan surukinsa na kwanaki uku?". Ya sani,abune me matuqar nauyin gaske,amma a yadda Ahmad din ya sauya a yanzu,ba kowa bane zai gane farat daya shine wancan almaz din ba,uwa uba sai Allah yayi wani abu cikin hikimarsa,ya hana sultane da duk wani me ruwa da tsaki ganawa da almaz a wancan lokacin,so da yawa basusan fuskarsa ba.....idan kuwa har mammina ta zama na farko da zata bankada maganar......zaiso haka,don zata burmawa kanta wuqa kakkaifa idan har hakan ta kasance. _Tofa......sheikh haisam........ko sultane zai yarda dakai?,ko sultane zai gasgataka?_ Tun daga bakin babban gate din daya mallaki manyan katangun masarautar ya sanya salaana ya saukeshi. Cikin nutsuwa da kamala ya dinga takawa zuwa cikin gidan,yana kuma gaisawa da dukkan hadimai,tun daga masu tsaron qofofi har zuwa masu kai kawo don tabbatar da komai na tafiya lafiya cikin masarautar dama wadanda uzurorinsu ne suka fito dasu. Komai yana nan akan tsari doka da qa'idar daya bayar. Hakanan kowa yana bakin aikinsa daidai da yadda ya dace. Ya sani komai zai tafi daidai din,dom fiye da rabin masu tsaron dukka sun fito ne daga qarqashinsa da kuma horonsa. Daga iyakar da yasan labarin shigowarsa masarautar zai iya kai mata......daga nan ya danna wani device don bawa mutanensa umarnin dauke hankula da masu kula da doguwar hanyar nan dake shimfide da interlocking,doguwar hanyar data zama kebantacciya da ba kowa ke da ikon binta ba,doguwar hanyar kuma da zata iya sadaka da sasannin sultane akhnan morsa mammina dama sashen baqi na musamman makusanta. A nutse ya bude qofar ya maidata kamar yadda take,ya kuma soma takawa a nutse yana kutsawa ciki. *A K H N A N* Bayan dukka tarin hayaniya da shiga cikin jama'a data jima batayi irinsa ba a yau.......ta zare jikinta daga cikinsu tun bayan sallar isha'i awa daya da rabi data wuce,ta kuma zabi dawowa dakinta da nufin tayi sallan magariba ta kwanta ko bacci zai dauketa.(haramunne bacci bayan sallar magariba,manzan Allah yace duk wanda yayishi bayan ya farka duk abinda ya sameshi ya zargi kansa). Alwala tayi kawai sannan ta rage kayan jikinta da taimakon birra kamar kullum. Ta tayar da sallah sannan ta idar bayan ta cewa birra bata buqatar kowa da komai. Da gaske take data fadi hakan,har yanzu wani nauyi takeji cikin zuciyarta,nauyin da batasan na meye ba......saidai bayan wucewar kowacce awa tana duban agogo.....kuma lissafin KWANA HUDU ZUWA YAU bai tsinke daga kanta ba,duk da qoqarin manta hakan da takeyi. Zaune tayi saman abun sallar bayan ta kammala sallar. Zuciyarta ta nace da tambayar "Kwanakin sun qaru" Idonta ta lumshe,tanason sanin ainihin damuwarta akan zancan. "Ba wanda ke maganar qaruwar kwanakin........ko sultane baiyi wani magana ba akai......" "Me yake damunki ne akhnan?.....me yasa kika damu da qarin kwanakinsa?.....me yasa kika damu da rashin jin motsinsa......da rashin jin komai ma daya shafeshi?" Zuciyarta ta jefa mata tuhumar data tilastata bude dukkanin idanunta tana kallon guri daya. Guri dayan da take ganin kamar a kallonsa kadai zata samu amsar tuhumar da takewa kanta da kanta. "Qila saboda shima ya nuna damuwa a kanta a sanda buqatar hakan ta taso......qila saboda yayi mata wani gagarumin taimako na kubutar da rayuwarta.....qila....qila qila din da yawa,saidai abu daya daya sanya komai dauke mata dif shine......qila tana jin wani kadaici.....wannan kular......wannan kulawar wadda ke mata kamanni da takura da tsanani a wasu lokutan duka babu su. Taji wannan sosai yau a jikinta,a taron walimar.....ta dinga jin cewa inda yana kusa.....inda yana tare dasu a sannan,qila lullubinta......rigarta data dinga zamewa dukka idanu da hankulansa suna kai. A yanzu fa?duk da kulawar birra.....duk da tarin hadimai amma sai takejin kaman ta rasa wannan bangaren. A hankali saita kifa kanta saman cinyarta,sai takejin kamar wani abu ta rasa me girma. Amma duk da hakan zuciyarta taqi amanna dari bisa dari,zuciyarta hujjoji kawai take bata mabanbanta. Hujjar an mata aure a sanda bata shirya ba.....hujjar aure da mijin da bata shiryawa ba.....hujjar zata bar qasarta......kamfaninta......sultane dinta dama komai nata. A yau da kanta ta hadawa kanta ruwan wanka,saidai rashin sabo dayin hakan ruwan yayi zafi da yawa harsai data fita ta qara tara na sanyi,shi kuma ya kusa salamcewa,a haka tayi wankan,ta fito kuma ta shirya cikin farar gown cotton me yankakken hannu,rigar da saboda rashin kaurinta kana iya hangen shatar bra dinta idan ka sanya idanu sosai. Iskar dake ratsowa ta tsakanin labulen dakin ya tabbatar mata hadarin dake ta hada kansa dazun a yanzu ya kammala wannan aikin. Ta shaqi iskar can cikin hunhunta da zummar fesarwa,saidai cak ta tsaya da iskar cikin hancinta saboda gauraya datayi mata da wannan qamshin. Wannan qamshin dai daya zame mata jarrabi.....wannan qamshin dai dake sama mata wata dukkan nutsuwa ya kuma birkita mata tunani a wadansu lokuta....wannan qamshin.......wannan qamshin,saita saki iskar da sauri,ta sake shaqar wata da hanzari da nufin tantancewa.....shin da gaske qamshin takeji ko kuma gizo ne hancinta yake mata?. Sake bude idanunta tayi tana sakin iskar a karo na biyu. Qamshin dai da gaske takeji,hancinta bai mata qarya ba a dukka karo ukun,to amma bataga koda alamar gilmawar kowa ba ballantana tayi tsammanin shine. "Shine wa?.....har kin fara imagination......anya bakya matakin farko na fadawa soyayya?" Zuciyarta ta sake tuhumarta. Siririn tsaki taja,duka wannan shirme ne takeyi,ta sani tun ba yau ba turaren ke mata dadi,kuma tabbas daga sanda ta mallakeshi shikenan komai ya qare,so ba wani hasashe ko tuhuma na daban. (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) Haka kawai taji sha'awar fita ta shaqi daddadar iskar dake kadawa a sararin subhana,siririn mayafi kawai ta aza saman kanta,saboda tasan inda zata tsaya din ba guri bane na shige da ficen kowa ba,ta zura lausasan bedroom slippers dinta da morsa safiyya ta tilasta musu zama dashi. Tana takowa a hankali tana sake jin kamar tana kusantar qamshin,a duk sanda ya jashi zuwa hunhunta kuma bugun zuciyarta ke tsananta. Wani memories suka dinga dawo mata a hankali. Ranaku irin wannan tsakaninsu na haduwar hadari da siraram yayyafi dama saukar ruwan sama me qarfi. Ta dinga tuna komai daki daki,kawai sai taji gabbanta suna saki a hankali. Sosai ya jawo cloak thobe dinsa yana tattareta cikin jikinsa sosai saboda iskar dake tasowa me qarfi,ya miqa hannu ya jawo amam din kansa yana lullube fuskarsa har zuwa kan hancinsa kamar yadda ya saba a yawancin lokuta. Yafi zabar barin zagayayyun idanunsa da hadaddiyar girarsa a waje akan barin dukkanin fuskarsa gaba daya. Sosai ta ware hannuwanta dukka biyun,iskar tana kada gangar jikinta sosai,tana kuma kwaso mata qamshi iri biyu tana dawo mata dashi hancinta. Na farko qamshin ta ne,wannan sassanyan qamshin na INCENSE BY KABO DAUGHTER daya kama jikinta sosai,0803 211 9803,cikin kowacce kafa ta jikinta ta saba jinsa,ya zauna ya manne da fatarta da wasu kalar turaruka da momma ta zube ake musu amfani dashi. Na biyun kuma wannan turaren dai....wannan qamshin dai da zuwa yanzu ya sanya ta fara tunanin ANYA BATA SAMU MATSALA BA?. Me yasa ko yaushe yake manne da ita?,me yasa ko yaushe take jinsa a kusa da ita?. Me yasa?.....me yasa?....me yasa?. Daidai sanda tambayar ke kaiwa qarshe cikin kwanyarta......daidai lokacin da wata qaqqarfar iska ta taso ta kuma yaye dan yalolon mayafin kan nata tayi gaba dashi,bata kuma damu ta bude idanunta ba ballantana tabi ba'asin mayafin,don tasan a duk inda zai sauka zai sauka ne a amintaccen gurin da zata dauki abinta tayi gaba. Iskar dake ratsata da qamshin dake shiga hancinta wani yanayi ne da batason ya katse mata. Da wani irin sanyi mayafin ya sauka saman kafadarsa sanda yake takawa da ginshirar nan tasa zuwa kebantaccen sassan sultane. Ya daga kansa a hankali yana duban kafadar tasa da dan mamaki shimfide saman fuskarsa na saukar mayafin. Hannu ya miqa a nutse don saukeshi,saidai sanda hannuwansa ke sauka akan kafadar sai idanunsa suma sukayi kyakkyawan gani da ita. Iska ce ke kada rigar jikinta kamar yadda take kada gashin kanta yadda taga dama. A nutse yabi siraran hannuwanta dake warwatse cikin iska. Da wani irin sanyi ya sauke mayafin daka saman kafadar tasa.....saidai a maimakon neman inda zai ajiyeshi.......sai ya damqeshi sosai cikin tafin hannunsa sulbin material din yana ratsa fatarsa. "Qila a irin haka?......a irin wannan yanayin tamim yasha ganinta har zuciyarsa ta fara saqa masa mummunan tunani?" Wani irin motsi zuciyarsa takeyi. Tana tsaye ne ba hijabi a jikinta.......tana tsaye a inda idan amintaccen hadimi hidimarsa ta kama ya biyo ta gurin xai biyo.....me zai faru idan haka ta kasance?. A hankali ya saki mayafin,ya kuma tashi yabi iska kaman yasan inda akeson aikashi,daidai sanda ya iska saman qafafunta......daidai sanda take bude idanunta da sauri jin saukar abu saman qafarta.....kuma daidai lokacin da yayi qoqarin sajewa da inuwar bishiyar dogon yaro dake gurin. Tabbas taga inuwar mutum.....sannan taga gilmawarsa......abinda ya hadu ya cakude mata a zuciya kenan,ya haifar mata da wani irin tsoro me nauyi,tsoron daya sanyata ta fara tafiya da baya da baya zuciyarta na tsananta bugu,tamim ya fado mata da komai daya faru,sai taji kamar tana shirin firgewa gaba daya. Ya gani,ya kuma lura da yanayin,abinda ya sanyashi takawa da wani irin zafin nama ta cikin shukokin,ya kuma zagaya ta bayanta ba tare da ta lura da faruwar hakan ba,saiji tayi tayi karo da wani abu,ta kumayi dungureshi ta baya. Tsoro fargaba da dimuwa ya sanyata juyawa da wani irin sauri numfashinta yana neman daukewa,tanason tantance waye?. Yadda ta juyo a razane ya tabbatar idan bai riqeta ba zatayi mummunar faduwa ne......tana juyowar ya sanya hannuwansa dukka biyun ya zagaye qugunta dashi. Firgici da lakarta data sabule sakamakon tsoro ya gusar da duk wani karsashi nata,wannan ya sanya ta samu kyakkyawan masauki cikin qirjinsa ba tare da tasan waye ba. Wani irin dumin daga anihin fatarta.....tudun jikinta dake tsakanin faffadan qirjinsa......wani irin dimautaccen qamshi dake fita daga sassalkar sumarsa dake barazanar rufe masa fuska sakamakon iskar dake kadawa da qarfinta.....wani irin sautin bugun zuciyarta dukka suka hadu lokaci guda suka soma ratsa fatarsa suna kaiwa zuwa ga kowacce jijiya dake jikinsa........wani irin abune yaji yana neman tafiyar da nasa numfashin,sai da yayi qoqarin riqeta da kyau gudun kada ta subuce ta kuma sulale.....sannan yayi jarumtar qwato numfashinsa daya qwace masa. *zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 08187255862 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 08187255862 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 11* Wani irin shuru ne ya ratsa a tsakaninsu,wani irin tsoro yake gani tattare da ita. Basu gushe ba tana cikin jikinsa suna musayar bugun zukatan junansu da kuma qamshin turarensu daya cakude guri guda ya bada wani sassanyan qamshi me narka zuciya. Yana jin yadda zuciyarta ke dokawa sosai,sai ya lumshe idanunsa a hankali yana mamakin tsananin tsoratar da tayi. Hannunsa ya sake miqawa ya riqo qugunta da kyau saboda yadda yaji kaman tana neman sulalewa qasa. Ya fahimci har yanzu bata gama nutsuwa ba,ya daidaita tsahonta sosai a jikinsa,sai ya aza hannunsa a hankali saman gashinta yana shafawa daga gaban kanta har zuwa gadon bayanta da yabi ya kwanta lambas kamar ba nata ba. "Relax......calm down.....nine......haisam ne" Ya fada da wata irin rarraunar murya da tayi wani irin sanyi kaman wanda magana takewa wahala. Yadda maganan ta sauka a kunnenta.......yadda qamshinsa a karon farko ya zama kusa da ita fiye da ko yaushe......wani irin kusa da ya zamana cikin kowacce shaqa da zata iya iska zuwa hancinta ta ratsa ta hunhunta ta kuma harba saqo zuwa kwanyarta. Ji takeyi kawai tana sake narkewa.......a yanzun abinda takeji ba tsoro bane zalla,wani irin tasiri ne me qarfin gaske. A sanda yake furta kalaman a jejjere......sanda yake maganar dan da kunnuwanta sai taji kaman duniyar tana juya mata a hankali,ko kuma an dauko wani abu me nauyi an azashi tsakanin tafi hannuwanta da tsokar zuciyarta. Lips dinsa ya cije a hankali,dumin jikinta ke ratsa kowacce gaba ta jikinsa......wani irin sauyi yakeji sosai tattare dashi,sai ya janyeta kadan daga jikin nasa,ya kuma tsugunna yasa hannunsa ya dauki mayafinta dake yashe a qasa ya wareshi sosai. Dogayen hannayensa ya daga saman kanta ya soma rufawa ba tare daya kalli fuskarta ba. "Ganganci ne wannan......ba guri bane kebantacce har haka ba" Ya qarasa fada yana yin taku biyu baya gami da bada tazara a tsakaninsu. A hankali da wani irin yanayi da kuma nauyi ta sanya hannunta tana tattaro mayafin ya riqe gam tsakanin tafukan hannayenta,sai kuma ta daga idonta a hankali tana ajeshi saman fuskarsa. A yauma mutumin hippodrome kawai take gani.....wannan me zagayayyun idanuwan masu nauyin gaske......idanuwan nan da suke da wani madaukakin tasiri a tattare da ita.....idanuwan da koda sau daya shape dinsu.....kyansu da yadda suke da wani irin zurfi basu taba bacewa dubanta ba. Kamar wasa....kamar almara saita gaza jurewa ci gaba da dubansa,ta zare idanunta gefe tana jin yadda zuciyarta keta birkicewa cikin qirjinta. Wani abu takeji can qasan zuciyarta. "Ya dawo kenan?,tun yaushe?,me yasa bai nemeni ba?......bai kirani ko sau daya ba tunda ya tafi me yasa?" Ta samu kanta da jerowa kanta da kanta dukkanin tambayoyin da a tashin farko wani sashen na zuciyarta ke tuhumarta. "Me yasa?......me yasa kika damu da dukka wannan?" Juya tuhumar kawai takeyi......juya tambayar takeyi cikin ranta tanason gano eh meye damuwanta?me yasa taji ba dadi. "Muje?" Ya fada da wani yanayi me kama da tambaya wani sashen kuma cike maganar yake da umarnin da taji yakai mata har cikin kwanyarta. Samun kanta tayi da daga qafafunta,a hankali ta juya tana saukesu da wani irin yanayi da har yanzu ya gaza barin jikinta. Batasan zai bita bane......sai jin takunsa tayi a hankali a bayanta. A qasa yake sauke idanunsa......yana qoqarin kammale ganinsa guri guda,saidai bai bada wata tazara me yawa tsakaninsa shi da ita ba. A hankali yayyafi ya fara sauka,wani irin yayyafi daya taho da qarfinsa,abinda ya sanyashi daga kansa kenan yana zubeshi akan bayanta da take takawa da wani irin sanyi da nutsuwa. Ida har idanunsa sun gane masa daidai,idan har yana iya.ganin zahiri to kamar ta tattare jikinta ne ta cure guri daya. Gabansu ya duba,akwai sauran taku kafin sukai ainihin qofar sashenta ta baya. Ya sani ya kuma gama fahimtarta,kamar batason ruwan sama ya tabata da alami,wannan yayyafin kuwa muddin yaci gaba da sauka da qarfi kamar haka ba abinda zai hana ta jiqe kafin su isa ko tayi damshi sosai. A hankali ya saki cloak thobe dinsa ya kuma zareta daga hannunsa,sannan ya taka ba tare da saninta ba ya budata sosai yana aza mata ita saman kafadunta. Har cikin qasusuwanta taji tsaiwarsa a bayanta. Har cikin b'argonta taji saukar cloak thobe din saman gangar jikinta,bata gama da wannan ba taji lallausan tafin hannunsa cikin nata yana qoqarin cusa mata gede da gefan rigar cikin hannuwanta gudun kada iska ya debeta ta fadi. Tana jin sanda ya zame hannun nasa bayan yaji alamun ta riqe,wani irin lallausan tafin hannu da ko cikin 'yan uwanta mata bata tabajin irinsa ba. Yana biye da ita tamkar wanda ke gadin wata tsadaddar kadara,dukkan dagawa da saukar fararen tas din qafafunta masu shige da nasa akan idanunsa ne,tanason waiwayawa ne......tanason juyawa ta kalli cikin idanunsa amma tana jin wani abu me nauyi kamar ba zata iya hakan ba. Dab da bayanta ya zura hannu sanda suka isa personal qofanta ta baya.......bata sani ba,ba kuma zatace ba taga ya fidda keya ya zura ya murza ya kuma bude sannan ya turata ta bude. Bata sake jin motsinsa ba saidai tasan yana tsaye a gurin,zuciyarta na sake zugata. "Kidan waiwaya ko sau daya ki kalleshi.....ki juya ki gani ko shurunsa ke yake bi da kallo". A wani irin sace ta saci kallonsa ta gefan idanunta,sai taga wayarsa ya fidda a aljihu yana latsawa,alamu kuna sun nuna gajeran saqo yake turawa. Haka kawai taji wani iri.....haka kawai taji ba dadi. Bata taba satar kallon d'a namiji ba a rayuwarta,saidai ita a saci kallonta harma ta hukunta mutum,amma a yau wai itace ke satar kallon wani?. Waninma da ba ita yake kalla ba?,kallon wayarsa yafi kallonta muhimmanci?. (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) Sai data shige duka sannan ta juyo a hankali,ta kuma sake wayancewa da dora hannunta saman handle tanayi kamar zata rufe qofar. Wannan karon kuma kai tsaye ta zuba masa dukka blue eyes dinta,tanason tabbatarwa da gaske wayar tasa yake kalla har yanzu?. Tabbacin kuwa ta samu,don yadda yake typing da sauri da sauri ya gaya mata wani saqon gaggawa ne zai aike. Sosai a yanzun taji ranta ya sosu fiye da dazun,sai kawai ta zabi rufe qofar wanda tana dab da hade gap don da yayi saura qofar ta qarasa kullewa ya daga kansa daga wayar,saidai bai samu daman ganin komai ba sai gefan fuskarta da blue eyes dinta guda daya. Murza muqullin jiki tayi tana jin zuciyarta tana mata zafi,sannan ta juya a hankali tana sake riqe cloak thobe don cikin hannuwanta tana damqeta da kyau kamar wani zai qwace mata. "Bai kula ba....bai damu ba?" Ta tambayi kanta tana jin ranta yana sake baci,saidai qamshin nan nasa da ya sanya takejin kamar yana dab da ita ya hana bacin ran nata yaci gaba. A parlor din da yafi kama da harabar da zaka zauna jiran neman izinin ganinta direct daga bedroom dinta ta iske birra. Ta sani koda kowa zai tafi birra zata zauna. Ta miqe tana nufota da zummar karbar cloake thobe din saman jikinta ta kuma taimaka mata ta sauya kayan jikinta,amma daga idanun da akhnan tayi tana duban birran da gane rigar waye a jikinta ya sanya birra janyewa da baya. Ganin birran ta fahimci abinda takeson fada kafin ta fadi,saita hadiye maganarta ta juya tana wucewa ciki. Ta jima zaune da rigar jikinta tana kallon yadda ruwa ke zuba ta glass door din data ratsa bangon,kafin a hankali ta zameta daga kafadarta ta miqe don hadata da 'yar uwarta. Wancan rigar daya bata aro wancan karon bata maida masa ba......a yanzu ga wata ta qaru,saita hadesu guri daya tana zubasu cikin wata 'yar jaka. Har yanzun koda rigar farko ma bata daina qamshin da takeyi ba bare riga ta biyu. *H A I S A M* Samun tabbacin ta rufe qofar ya sanyashi maida wayar aljihunsa a hankali,ya juya a nutse yana takawa zuwa sassan sultane da yake iya hangowa dab da shi. Tun daga qofan farko amintattun hadiman me martaba suke masa iso. Shiga shiga shiga yau sai gashi har qaramin parlor dake manne da bedroom dinsa,parlor din da daga shi sai matansa sai yaransa duk iya tsanin shaquwarka dashi batakai ka iso nan ba. Da sallama ya shiga,duk da bai sameshi zaune a gurin ba,sai yayi tsaye yana goye da hannuwansa a qirjinsa yana qarewa parlor din kallo a nutse. Mutum har mutum......mutum ma basarake,me jagorantar dubbai kuma miliyoyin al'umma,ya sarrafa ko wane lamari da sha'ani,amma ya wayi gari cikin juyawa da kuma makircin mace qwaya daya tal. Ya kwashi shekaru cikin duhu,cikin rashin sani da makanta me tarin yawa. "Yaya zaka tsaya muhammad?,shin ka manta a muhallin mahaifinka kake?" Muryar sultane ya katse masa dogon nazarin da yakeyi. Wannan murmushin......wannan murmushin mai cike da tarin nutsuwa ya sakar masa. Cikin girmamawa ya furta. "Barka da fitowa". "Barka kade Muhammad.......zauna" Sultane ya sake masa tayin zama sanda yake zama shima saman kujerar. Cikin mutuntawa haisam ya bashi hannu sukayi musabaha me dan tsaho,sultane yana tambayarsa batun tafiyar. "Tafiya ta kammala.....ta kuma zo da bayanai na abubuwa masu nauyi da girma" Sosai maganar ta sauka a zuciyar sultane cikin wani gurbi na zuciyarsa,sai yaji wani abu yana lullubeshi kasalarsa tana ninkuwa. "Allah ya tabbatar da dukkan alkhairi" Ya fada haka kawai yana jin zuciyarsa tana laushi. "Ameen ameen" "Dukka hadimai sunyi nisa da gurin hidimarsu......akwai duk wani nau'in abu da kake buqata kaci ko kasha daga can" Murmushi haisam yayi kadan,ko yaya mutum me karamci yake sai ya nuna karamcin nan nasa. "Alhamdulillah,godiya nake" Ya fadi yana sake nuna girmamawarsa a gareshi,shuru ya ratsa na wani dan lokaci,sultane yana jin wani nauyi yana jin akwai abinda ya kawo haisam din,akwai abinda haisam yakesonyin magana akai amma kuma shima ya gagara tambayarsa. Gyaran muryar haisam taja hankalinsa. "Allah ya taimakeka.....nace ayimin afuwa,na nema ganinka a lokacin daya kamata ace kana hutawa......Musamman kwana biyun da akace bakajin dadin jikinka". Murmushi yayi mai cike da dattako. " A duk sanda d'a keson ganin ubansa daidai ne,hakan bazai zama laifi ba sam sam". "Haka ne.....akwai wata gaskiya ce data jima tana boye......kuma yanzu lokacin boyewarta ya wuce" Yayi maganan a hankali yana duban sultane. Sanyaya jikinsa yayi,zuciyarsa tana rawa kadan. Fatansa kawai Allah yasa ba wani mummunan abu bane.......fatansa kawai Allah yasa koma meye bai shafi aurensa da akhnan ba. "Ina jinka muhammad" Ya fadi yana sallamawa cikin ransa. "Ni ba malami bane kawai kamar yadda ka sani,kamar kuma yadda kowa yake kallona.......ina da wani aiki na daban da nakeyi tun daga qasata". Yakai maganan qarshe shuru yana maye gurbin dakin. *zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 08187255862 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 08187255862 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 12* Wani irin shuru da ya wanzu saboda idanu kawai da sultane ya zubawa haisam. Yana zaton zaiji tsoro ko wata fargaba amma game da maganar haisam da tazo ba zato ba tsammani......yana zaton zaiji wani tashin hankali ya sauko masa amma ba wani sauyi da yaji. "Na sani......na sani muhammad,koa hankalce bakayi kama da malamin nan ba.....malamin da baida aikin yi,malamin dake komai kara zube ba,na karanceka kafin jawoka jikina.....na karanceka sosai kafin na sanyaka tsakiyar ahalina.....amma ban sani ba,na karanceka gaba daya ne ko bai karanci komai daga kai din waye ba". Yayi maganan da wani iri laushi da hope sosai a muryarsa ba. "Baka karantani duka ba.....saidai ina me baka albishir ba zakayi nadaman sakani amana cikin ahalinka ba......ba wannan ne abu mafi muhimmanci ba sultane......aikina ya ratsa ta wani bigire.....aikina ya biyo takan wani muhimmin abu cikin rayuwarka". "Ban damu ba muhammad.......ban damu ba,nagartarka kawai nakeso,muddin ta tabbata bani da matsalar sanin waye kai ko meye aikinka har qarshen numfashi na". Wani nauyi.....nauyi haisam yaji sosai saman zuciyarsa. Ya Allah.....wanne irin yarda da aminci ne wannan?,wacce irin qauna ce wannan?. Ya rabb,kada ya bashi ikon cutar da sultane ko sabawa zatonsa. "Wanne abune haisam?.....sanar dani" Sultane ya fada yana gyara zamansa. "D'anka.....d'an ahmad" Idanu sultane ya zuba masa ya kasa cewa komai. "D'ana ahmad?,d'a kuma jinin farko na safeena da muhammad hammud?" Kai haisam ya jinjina masa yana kallon yadda wasu emotions ke tasiri a tattare dashi. "Shi......yana raye,bai mutu ba". Wani irin abu sultane yaji ya doka tsakiyar kansa,sai ya dinga jin maganar haisam tana amsa kuwwa a kunnensa. "Yana nan a raye,lafiya qalau" Ya sake fadi don ya bawa sultane qwarin gwiwar tambayarsa ko sau daya ne. "Yana ina muhammad?,ahmad fa?,ba irin neman da bamu masa ba,ahmad hatta da safeena duk da zurfin haqurinta ta saddaqar ta rasashi....ahmad dai?" Ya tambaya cike da shakku. "Ahmad yana raye.....ubangiji yaga dama ya raya abinsa". Yayi furucin a tausashe. Zumbur yaga sultane ya miqe,ya kama hannuwan haisam sosai cikin nasa yana duban idanun haisam din da nasa idanun,idanuwan da suka cika sosai da ruwan hawayen da jarumta irin nasa ya hana musu kowanne tasiri. "Ya girma ko?,yayi hankali haisam?,kaini na ganshi,kaini naga ahmad,inama ace safeena tana raye?" Wani irin tausayinsa me narkar da zuciya ne ya saukarwa haisam,sai ya kama hannuwansa shima,yayi taku uku ya matsa dab da sultane din don bashi kafadar da zai jingina ya samu sassauci. Kamar yasan me manufar haisam kuwa,sai ya rungume kafadar haisam yana sauke wani irin numfashi,wani numfashi me tsananin nauyin dake bayyana girman tsananin da zuciyarsa ke cikin tsahon shekarun. Ya tabbatar inda gama garin namiji ne sultane din kuka zai fashe dashi. Ashe duka shekarun nan yana rayuwar kawai,yana maida komai ba komai ba?,amma akwai ciwon rashin ahmad din tattare dashi. Yadda yaji jikinsa ya fara kyarma sai ya kamashi a nutse ya zaunar dashi,don yasan zuwa yanzu abinda ya bawa me wada ya dinga shayar dashi ya ratsa jikinsa sosai. "Akwai shaidu ga gwajin qwayoyin halitta.....bari na gabatar maka dasu" Caraf yaji sultane din dake ajiye wani irin numfashi ya riqe hannunsa "Ba buqata haisam.....na tabbatar yadda akhnan ba zatamin qarya ba,ba zata cutar dani ba hakazalika kaima". Maganan ya sanyashi dakatawa daga warware takardun yana duban sultane da girman yadda da amincewar da yayi masa. *M A M M I N A* Ji da ganin komai take kamar a mafarki,an aurar da falaak ana shagulgula dukka cikin gidan ita bata sani ba? Wai yaushe?,yaushe haka ta faru?,yaushe tayi wannan baccin?,yaushe tayi sake haka..yaushe al'amura suka fara mata sako sako?. "Bai kamata kici gaba da zama ba komai yana zamewa daga hannunki......bai kamata ki zauna har sai an gane akwai wata babbar barazana data tunkaroki ba". Ta fadawa kanta da kanta,abinda ya bata qwarin gwiwar miqewa,saidai kuma tana miqewar ta koma ta zauna saboda wata bahaguwar faduwar gaba daya ziyarceta. Tunawa tayi a yanzu kamar bata da kowa......ba wani da zatace ya rage mata idan ka dauke tamim qarami.....ba tamim babba,ba babban tamim dukka,salihi.......naziru....bashir.....lawan.....ashiru.....dahiru......rabi'u.....labaran......kanzu.....dan tala.......habu dukkaninsu bata da masaniyar ina suke?. Qasqantattun bayinta da ba wanda yasan girman kusancin dake tsakaninsu sai ita. Yan shige da ficenta masu mata kowanne aiki hankali kwance. Abinda yafi bata mamaki bataga kowa yayi noticing bacewarsu ba,ba wanda taji yayi cigiyarsu,wannan ya dasa mata tsoro tayi magana akai. Tayi magana a kansu tace me?,tace sun b'ata?,me yasa ba wanda ya gani sai ita?. Motsawa tayi tafisu tana fado mata a rai,ta sake juyawa tana qwalawa hadimarta kira. "Ki shaidawa tafisu ina buqatar ganinta a yanzu yanzu". " An gama" Ta fada tana miqewa cikin qasan ranta tana gulmar mammina din. Sumammakin data dinga yi a jiya tamkar me cutar farfadiya.......kamar wadda bugun jinnu suka kama,sai gashi daga tsakanin jiya zuwa yau din ta wani fede tayi fayau da wata irin ajiyayyar rama. Ta zurfafa tunani tana lissafin jimawar tafisu kafin taji sallamar tafisun. Kai ta daga tana dubanta yadda take takowa da wani rashin kuzari,kafin ta qaraso gabanta ta zube kaman yadda ta saba tana gaidata. Batabi takan gaisuwarta ba......sai magana data fara cikin izzar nan tata. "Wanne sabon salon tsari ne kika ajiyewa kanki?,yin nesa dani a sanda yafi cancanta ace kina kusa dani?". Kai kawai tafisu ke mirginawa. " Allah ya huci zuciyarki ranki ya dade,na shiga wata dimuwa ne kan abinda ya sameki a jiya,abinda har yakai ga rikicewar cikina na barke da zawo,dole.na kasance a shiyyata kusa da bayan gida". Shuru tayi tana kallonta,kafin taja numfashi. "Ko meye ya faru dake.....bana buqatar wannan nisan.....inason a shirya komai,kyaututtuka na alfarma da bajinta,inason na shiga hidimar bikin gidan nan ayi komai dani,a waremin suturar alfarmar da zanyi amfani da ita" Shuru kadan tafisu tayi kafin ta amsa da "To ranki ya dade" Sannan ta yunqura tana miqewa kamar wadda bata da cikakkiyar laka a jikinta. (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) Inda giwa zataji......inda giwa zata aminta da ta yarda taci gaba da zamanta kawai a shiyyarta. Iya yadda tayi muzu muzu kawai zata zama wata ayar tambaya ta daban a kanta a idanuwan al'umma,wanda duk yadda takai ga yin ado da kwalliya don ta boye ta sani ba abu bane da zai iya boyuwa ba. *A K H N A N* Juyi kawai takeyi cikin bargon tun da ta bude idanuwanta daga bacci har kawo yanzu da azahar ta gota ake kuma shirin gudanar da yininsu na al'ada wanda aka yishi akan wani tsari me kama da zamani zamani. Babbar makeken filin dake qarshen gidanne,morsa safiyya ta sanya aka qawatashi da dukkan wani ado me daukan hankali nutsuwa da kuma dacewa. Tana daga dakin a kwance,amma tana ji a jikinta taron yau yafi na jiya,saboda yawan hayaniya da takeji daga can sasanni daban daban na gidan. Idanunta ta sake maidawa ta lumshesu,bata kuma budesu ba,batasani ba ba kuma zatace ga taqamaime ko ainihin abinda yake damunta ba. Abu daya zata iya dorarwa.....tana jin wani d'an baci bacin rai a tattare da ita,musamman idan ta lumshe idanunta ta hangi sanda ya zubawa wayarsa idanu ba tare daya damu da kallonta ba. Ita din dai da ya kwashe kwanaki hudu zuwa biyar bai ganta ba.....bai nemeta ba,ya dawo kuma baice gashi ya dawo ba....... Abu na biyu wani irin fayau take jin zuciyarta,tamkar dai akwai wani abu me girma da aka cire da yabar mata fili har haka. Qamshin nan na jiya,shine har yau yake mata yawo a hanci,duk kuwa da cewa tayi nesa da dukkan rigunan nasa guda biyun gaba daya. Hairaan ce tayi sallama gami da turo qofar dakin gaba daya tana shigowa,idanunta akan akhnan,bayanta kuma shehnaz ce rungume da wasu kaya da akhnan batasan na meye ba. Waya take amsawa,amma itama akhnan din take kalla. "Biftu.....lafiya dai ko?" Ta tambayeta cikin nuna kulawa. Sai data aza idanunta akan shehnaz sannan ta soma ture duvet din tana qoqarin zama. Batason ta nuna duk wani weakness dinta,saboda tasan muddin shehnaz zata gani ta banu ta lalace. Jiya da qyar ta barta ta runtsa,tunda ta shigo dakin wanda a nan ranar shehnaz taga daman kwana ta hanata sakat. Motsi kadan sai tace. "Wallahi qamshin turaren sheikh Muhammad nakeji" Ta sanyata dukka ta tsargi kanta,yayin da taji ta fara kaiwa bango da yadda take maimaita qamshin turaren haisam din. Wanne irin sani ta yiwa qamshinsa?,a ina tayi masa wannan kyakkyawan sanin data dameta da maganar qamshin turarensa?. Sanda ta fito daga sauya jiqaqqun kayan jikinta tana ware gashinta yasha iska shehnaz ta sake maimaitawa a karo na babu adadi. "Wannan turaren na shiekh.....basan daga wacce aljannar aka sauko masa dashi ba.....ko yaya yake sai ya nun......" "Shehi!" Ta fada da siririyar muryarta wadda ke tsike da maganganun shehnaz din. "Ni ko ke wani zai iya fita ya barwa daya dakin nan ya kwana shi kadai?". "Daga ni har ke ba wanda zai barwa wani dakin nan......wai kwana nawa nema ya rage tsakani biftu?.....saura kwana kadan kwananki ya qare a agadez fa". Maganan ya doketa sosai,don sai a sannan ma abubuwa da yawa suka dawo mata. Ta watsawa shehnaz harara. "Waye yace miki zan tabbata ne a can?,inbar sultane in bar sahel couture?" Dariya sosai shehnaz ta dinga yi. "Kinga idan zaki shirya gwara ki shirya fa.....sai yadda kawai ta yiwu,sai abinda mijinki yace". " Mijinki" Kalmar ta dinga maimaituwa cikin kanta. Wannan maganan da sukayi da shehnaz,da kuma wannan mayen qamshin da wanka ma bai hanata jinsa a hancinta ba su suka hadu suka nuqurqusa karsashinta. "Idan ya dawo.....me yasa bai nemeni ba?" Ta tambayi kanta da kanta yafi sau shurin masaki. "Birra tace baki fadi me dame kike buqatar a shirya miki ba.....me yasa?" Hairaan ta tambayi akhnan din tana dubanta. Duban hairaan kawai tayi,don ita ta manta ma da batun wani hada kaya,tafiyan ce wai da gaske?. "Komai ma.....kawai komai ma da zata iya" Ta amsawa hairaan tana sauke qafafunta qasa. "Shehnaz ki taimakawa birra ku hada abinda ya dace" Hairaan ta fada tana jawo jakar da tasa aka shigo da ita dazu tana nufar qofar fita. "Ta zama ta zama.....aure ibada" Shehnaz ta fara rera waqar da akhnan ta tabbatar idan ta biye mata rigima zasuyi,kawai sai taji kewar AISA ta kamata. Tunda AISA din ta tafi basuyi waya ba.....sannan duk wannan hidimar da ake ko daya bata kirata ba bare ta samu daman zuwa taron. Shin meye ya tsare AISA din?. _oho......muma bamu sani ba......amma dai.....muje zuwa_ Cikin abinda ya rage mata tasaki kuka ganin yadda qamshinsa da tunaninsa ke maqale a zuciyarta lokaci bayan lokaci kadanne. Ta lumshe idanunta ta kira sunan Allah har batasan adadi ba. Guri ne da aka masa wani irin tsari,taro ne na manya,manyan mutane dama matan masu hannu da shuni da kuma fada a ji daga agadez da wajenta. Kai kana kallon gurin basai an gaya maka ba zakasan cewa taro ne masu hankali aji da kuma taqama da mulki da tarin dukiya. Ba kide kide.....ba maza ko daya,daga masu daukan hoto har masu serving abinci ga mutanen dake zazzaune saman carpet carpet na alfarma dake gurin duka mata ne. Duk da yawan al'ummar amma ba cikowa ba hargowa,wadatacciyar iska ke kadawa a gurin wadda hadarin daya hado ya baje zuwa sanyi ya bada gudunmawa me kyau wajen daidaitar yanayin gurin. *zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 08187255862 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 08187255862 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 13* Ranace me dumbin tarihi da martaba ga familyn DIORY HAMMANI na aurar da diyar safeena da safiyya,kintsatsen family din da nutsuwa ilimi da kamala suka cikashi,abinda ya taimaka gurin qayatar gurin kenan. Idan ka hangi morsa safiyya a daidai lokacin......kyautar kudade da sulallar da taketa yi......farincikin dake shimfide saman fuskarta zaka rantse da Allah bata taba baqinciki ba a dukkanin rayuwarta,ko kuma bata ma taba sanin mene baqincikin ba. A yau tana jinta kamar wadda aka bawa sabon rai dama rayuwar gaba daya. Hakanan ta bangaren nannie......abinda ke kai kawo a ranta yadda suka aurar da falaak da akhnan da aurenta ya kusan zama barazana.....Allah ya kawo lokacin kauda aisa don shehnaz da nata maganan a hannu. Tsakanin su biyun saika gaza tanta ce wace uwar akhnan da shehnaz?. Daya bayan daya hadimai daga sassan mammina suka fara shigowa,dauke da akwati kwati kanya masu kwana hudu dake lullube da wani kyakkyawan yanki. Wani shuru ya ratsa gurin kadan,shurun da yazo ne kawai cikin arashi,sai kuma yayi daidai da shigowarta. Da dukka izzarta take takowa "Dole su gani.....har yanzu ni giwa ina nan,ba wani abu daya canzani" Tayi maganar qasan ranta. Cikin zuciyarta tana jin qilan akwai wannan wanda ke farautarta a nan gurin....idan ma maqiyanta suna kallonta....tabbas zata nuna musu ko giwa ta fadi tafi qarfin wawa. "Nice me gayyata......bawai wadda ake gayyata ba" Ta fadawa kanta da kanta tana sake kambama kanta tare da bawa kanta qwarin gwiwa Daga falaak har akhnan din,a yau sai kamanninsu suke nunawa,kamannin da suke tabbatar da nasabarsu da SULTANE MUHAMMAD HAMMUD......Kamannin da suke nuna su din jinin MASARAUTAR AGADEZ ne na gaske. Daidai lokacin da yake zaune shida sauran 'yan shidan. Khadeem....mutallab.....amjad,omar,maleek,naseeb saishi na bakwai daya fita kadan daga da'irarsu yayi relaxing a wata kujera daban dake nesa kadan dasu. Sosai ya narke cikin kujerar,dukka idanunsa suna zube saman mini system din dake girke a gabansa a kunne. Tun jiya ba tare da sanin kowa ba,daga shi sai abeer ya sanya aka maqala na'urar tsaro a kowacce kusurwa ta gurin da za'a gabatar da taron. Yayi ne da nufin samar da cikakken tsaro.....yayi ne don ya tabbatar da cewa yau din gidan ya zamana cikin tsaro. Musamman yau din data kasance sultane ya zabeta,ya zabeta a matsayin ranar da haisam da kansa zai gabatar da ahmad cikin iyalinsa. "Bansan ko akwai wani shirin ba,bansan ko akwai wani tsarin ba,amma inaso kayimin alfarmar gabatar da ahmad cikin iyalinsa a karo na biyu.....a daren ranar lahadi,inaso a gaban kowa,kowa ya shaida dawowarsa......koda kuwa ka boyemin,jikina yana bani batar Ahmad tana da sila......tana kuma da dalili ba haka siddan ta faru ba.....na kasa nutsuwa muhammad,idan na kwanta fuskar ahmad yana qanqani nake hangowa". Sosai wani abu ya narke a zuciyar haisam din,yasan wannan ciwon a murya da idanun Nanay dinsa.....wannan dalilin ya sanya yakejin lokaci kamar yayi tsaho.....lokacin da zai bata albishir din safeenarta tabar wani reshe.....reshen da gata a gabanta ya kawo mata. Haka kawai yaji yana ra'ayin monitoring gurin da kansa,amma kaman bazai iya ba saboda gajiyar dake nuqurqusarsa kwanakin. Daga ahmad har Muhammad basason yayi nisa dasu,sukan kashe Lokaci sosai tare dashi,wannan ya sanya saboda ya fara shiga tsakaninsu sosai,suke wani mugun bash in respect tamkar babban wa da kowannensu ya rasa bai samu ba. Ya zauna gaban masarrafin cameras din,ya kuma bude kowacce shiyya,amma sai ya samu kansa da kashe kowacce camera ya miqawa abeer dake kebance a daki shi dasu beeno,ya zabi fuskar camera qwaya daya......fuskar camera da ta nan ya hangi takowarta tana isowa gurin zaman da aka tanadar musu. Lafiyayyar atamfa ce a jikinta me wani irin kwantaccen launi mara hayaniya ko saurin jan ra'ayi,saidai kuma yadda ta kwanta a fatarta shine abu na farko da zai fara fusgar hankalinka fiye da kima. Wani irin sassanyan kyau da karon farko idanunsa suka fara sauka akai......wani sassanyan yanayi......basaraken jikin nan saye cikin atamfar hausawa.....atamfar data zama daya daga cikin suturun da yayi research akai na yankin africa da yaji yana burgeshi sama da komai. (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) Atamfar dai aka warware,aka dorata daga saman daurin dankwalin kanta wanda aka matse da clip don kada ta sauka,mayafin kuma ya watsu a gadon bayanta da sample din shigar suturar ALKYABBA. Idanunta.....labbanta.....dama fatarta dukka sunyi wani fresh......blue eyes dinnan sunyi fayau,don ba wani makeup saman kyakkyawar fuskarta sai anihin zallar madarar kyan da duk motsawar da zatayi yake magana akan kansa da madaukakin sauti. Idanunsa ya lumshe a hankali yana jin wasu abubuwa suna spark cikin kansa,yaja boyayyen numfashi ya aje yana sake ware idanunsa daidai sanda take dab da abun zamanta. Idan har ya gani daidai kamar wadannan siraran labban sun furta "Bismillah" Ne,sai yaji wani dadi yana sauka har qasan ransa da zuciyarsa. Siraran zara zaran fararen yatsunta da wani lalle me azabar ja ya yiwa ado me fusgar hankali ta sanya tana tattara lullubin saman kanta zuwa gaban rigarta da dinkin ya rufe komai ruf,saidai hakan bai hana bayyanar tudun qirjinta ba daya zauna dasss kaman zanashi akayi ba halitta ce cikin qirjinta ba. Wani abu me qarfi yaji ya sauka masa. "Me yasa ba hijab ba?" Ya yana motsa labbansa da qarfi,omar da yadanfi kusa dashi ya waiwayo da hanzari. "Captain.......magana kakeyi?". Wadannan tsumammun idanun nasa ya daga a nutse ya zubewa omar su,kallon da ya sa ya omar janye dubansa daga kansa,bai kuma sake tankashi ba ya koma cikin hirarsu dasu naseeb. Sake janye idon nasa yayi,yana sane ya yiwa omar irin wannan kallon,ya fuskanci tun dazun akwai wani magana ne cikin bakinsa.....ko a dazun bai shirya doguwar magana ba bare yanzun da yakejin komai yana sauka daga ainihin saitinsa daga kwanyarsa. "Halal.....halal ce" Zuciyarsa ta fada masa a sanda yayi zooming fuskarta dab da dab. Daga nan inda yake yana iya hangen wani abu me nauyi cikin idanunta.....kamar kawai qarancin walwala saman fuskarta ta,kamar akwai abinda ke damunta can qasan ranta,hasalima wayarta na tsakanin yatsunta tana jujjuyata tana wasa da ita kawai,bata iya daga kai ta kalli mutane yadda ya kamata. Haka kawai yaji sha'awar yayi magana da ita......a kwanakin nan aduk sanda zai tunata yana tunata ne da TAUSAYI. Ya yadda cikakkiyar marainiya ce ita gaba da baya ba tare da ita tasan marainiyar bace a karan kanta. _smile.....its a sunnah_ abinda ya rubuta kenan ya kuma aike mata ya saqon karta kwana,sannan ya maida wayar gefansa ya ajiye yana maida kallonsa ga allon system din. Akan idonsa saqon ya shiga. Yayi qara kadan,tayi kaman ta share,sai kuma yaga ta bude. Reaction nata ya nuna sosai......wani irin reaction daya nuna zallar mamakinta a fili. Wadannan blue eyes din tadan bude kadan kafin ta maidasu daidai,ta sake dago wayar daidai fuskarta da alama tanason tantance number waye?. Murmushi kawai ya subuce masa ba tare daya shirya hakan ba,yanayin sai yaji ya masa dadi. Tsokana......a tsakaninsa kawai dasu maleek irin haka take faruwa.....yau ne karon farko da tsokana ta hadashi da wani jinsi daban ba nasa ba. Wayar ya sake dauka,ya sake rubutawa a gajarce. _smile mana please_ a wannan karon murmushinsa me sauti ne,saboda yadda yaga gaba daya ta diririce tana waige waige tana kuma sake kallon fuskar wayar tata,kafin ta tabo birra dake gefanta ta qaraso ta kuma rusuna ita kuma ta shiga nuna mata wayar birra tana kalla tana saurare. Ya fahimci me takeson sanyata tayi sanda ta damqa mata wayar,ta koma ta zauna,saidai duk da wayar tabar hannunta yaga alamar bata nutsu ba,tanata rarraba blue eyes dinta kawai tsakanin jama'a,sai ya sake sauke murmushi yana jawo wayar ya danna Stwiched off ya kasheta gaba daya. Sai a sannan yaji yadda parlor din ya dauki shuru,ya aro nutsuwa ya azawa fuskarsa kafin ya daga idanunsa ya bisu da kallo daya bayan daya. Kowa kawai idanunsa yana kanshi,daga sanda yayi wannan murmushin me sauti sai ya dauki hankulansu,yadda yaci gaba da murmushi kadan kadan kuma ya qarasa kashesu gaba daya. Yana da kirki sakewa da abokansa......amma ba kasafai zakaga yayi murmushi a jere har sau biyu haka ba. "Lafiyanku?" Ya maze yana jefa musu tambayar "Kai zamu tambaya captain,ko yau ka fito daga daki a daren farkonka iyakar murmushin da zaka yita yi kenan" Amjad dan kai tsaye ya fadi yana miqewa ya dauki wayarsa,don ya tabbatar tunda ya fadi wannan maganar akwai case ci gaba da zamansa a gurin. Wani nauyi yaji ya kamashi,saidai bai bari sun fahimta ba ya bisu da tsaki,ya maida hankalinsa ga system din,yana jin kamar bayaso amma haka ya kasheta yana fadin. "Yana daga cikin kyawun musuluncin mutum,yabar abinda babu ruwansa". *_KOMAI NISAN DARE_* *_KOMAI NISAN JIFA_* *_KOMAI GIRMAN GONA........_* *AGADEZ PALACE* *sultane muhammad hammud meeting room* *zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 08187255862 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 08187255862 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 14* Saman kujerun da aka tanada cikin kebantaccen dakin ganawar na musamman. Dauke yake da Wazeer,babban alqali na jaha,wali,galadima,shugaban limamai,da shugaban malamai. Ta daya bangaren kuma tsoho ne me ran qarfe wato kakan safeena wanda shine kan zuri'ar diory hammani family a yanzu gaba daya wato mamman hamza,da 'ya'yan 'yan uwansa da a yanzu suke taka matsayin iyayensu ne a wajen mamman hamza din. Daga bangaren sultane kuwa,yakumbo ce,sai qannanesa guda biyu da suke zaune a diffa da zinder,sai nannie sai kuma morsa safiyya da mammina dake zaune gaba kadan da morsa din cikin jin izza tare da mamakin dalilin wannan hadin da wannan kiran da sultane din yayi musu. Kusan duk wani gaishe gaishe an kammalashi,sarkin malamai ya gabatar da addu'o'i sosai,sai shuru daya biyo baya kowa yana tattara hankalinsa ga sultane. "Alhamdulillah......Alhamdulillah......alqawarin Allah baya tashi.....alqawarin Allah baya sauya ba,haka rabon bawa baya wuceshi,ban taba zaton wannan rana zata zo,ban taba tunanin zata riskeni ba......amma cikin hukuncin Allah bayan shekaru masu yawa da fidda rai sai gashi rabona ya dawo zuwa gareni...........muhammad,ku qaraso kaida ahmad" Sultane yayi maganan yana kallon wani guri. Labulen dake wajen ya yaye kadan,ahmad ya fara yowa gaba,haisam na biye dashi,dukkaninsu cikin nutsuwa da kamalar data qara musu kwarjini. Shigar dake jikin almaz a yau din ta sake saka wani irin kwarjini a fuskarsa da kamala cikin halittarsa......irin wannan kwarjinin da duk wani ahalin sarauta ke dashi,a yau kamar an sauya fuskar almaz din,kamar yaune ranar farko da aka masa wanka da ruwan kwarjini irin na ainihin jini da 'yan gidan sarautar AGADEZ,kwarjinin haisam kuma sai ya sake haskashi da wani irin yanayi da ya sanya kowa zuba masa idanu. Kamar an dauko babbar mota an jibga mata tsakiyar kanta.....kamar wadda jirgin sama ya daki tsakiyar qirjinta.....kamar wadda akayi dauka aka wujijjiga aka jefo daga saman wani dutse ko tsauni me tsananin tsaho haka taji yanayinta ya koma. Batasan ta miqe tsaye ba har sai da suka hada idanu da haisam. Wani irin miqewa ta tsananin razana da firgici........amma kuma saita maye gurbin hakan da nuna alamun farinciki da tsananin mamaki. "Almaz......ahmad" Tayi hanzarin gyara sunan tana soma takawa tana nufarsa. Cak ya tsaya yana dubanta......abubuwa da yawa suna dawo masa saman kansa. Banda haisam yace kada yayi komai.....kada ya sake ya aikata komai wanda yake ba daidai ba,ba shakka ba abinda zai hanashi kwasheta da mari sannan ya kwasheta ya watsar guri guda. Kanta tsaye ta rungumeshi tana sakin qirqirarren kukan da a zahiri yake cike da tsoro da kuma fargaba. Tsoron tonuwar asirinta......tsoron kada wani abu daban ya biyo baya......tsoron faruwar wani mummunan abu na yayewar sirrinta. Idanu kawai morsa safiyya ta zuba musu shida mammina din,zuciyarta na wani irin tsalle a qirjinta,wani yanayi takeji da yake sake bata tabbacin lallai shi din jinin safeena ne. Sai ta miqe tsaye cak,tana jin qafafunta suna rawa ta qarasa gabansa. Ta yarda da sheikh haisam har fiye da yadda ta yarda da kanta,tunda ta gansu tare ta tabbatar akwai wani abu,to amma tanason ta bawa zuciyarta tabbacin da babu shakka ko kokwanto a kansa. A hankali yayi taku biyu yaja baya yana raba jikinsa dana mammina.......sannan kuma ya juya kansa gefansa yana duban morsa safiyya dake tsaye tana kallonsa da idanunta da suka cika taf da qwalla. Haka kawai yake ganin wasu abubuwa tattare da ita,haka kurum duk dabai shaida wace ba yakejin wani strong connection daga idanunta zuwa nasa. Wani nutsuwa da kuma wani kalar aminci yana baibayeshi. Taku uku ta qara,ta iso gabansa,ta miqa masa hannunta,saiya bi hannun nata da kallo "Hannunka" Ta fada tana sakin murmushin dake cakude da qwalla. Bai musa ba ya miqa mata hannun nasa,ta riqe cikin nata ta soma janye hannun rigar dake jikinsa. Hannunsa ta soma jujjuya tana neman abinda takeson gani. Ta sake juya hannun zuwa saya b'angaren,take idanunta suka gano mata abinda takeson gani din. Wata runguma me qarfin gaske takai masa tana sauke wani nutsatsen kuka me taba zuciya,sai kawai ya samu kansa da riqeta sosai cikin jikinsa. Wani abu yaji yana motsawa har qasan zuciyarsa.....wani irin motsawar zuciya da zaije bai taba jin emotion irin wannan ba. Karyewar zuciya ya dinga ji kamar shima ya saki kukan,saidai tuni ya horu ya kuma karantu akan dabi'un basarake......ya kuma haddace kusan dukkan al'adu da dabi'ar masarauta. "D'ana ne......ahmad ne.....ebba na.....ebba masoyi" Sunan yaji ya harba cikin kansa.....sai yaji wata wuta ta kawo cikin kansa,ya daga idanunsa yana saukewa a kanta still duk da tana jikinsa. Kamar yana tuna sunan.....kamar yasan sunan a wani mafarki daya taba yi.....kamar yasan sunan a wata rayuwa daya taba yi a baya. (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) "Ki zauna safiyya,kiyi haquri" Nannie itama da idanunta suka cika da hawaye ta fada bayan ta miqe tana kaman morsa safiyya ganin yadda kukanta yake qara yawa ainunn,har dukka jikinta yana amsawa. Wani irin sanyi takeji suna bin dukka gabbanta.....wani irin yanayi da ba zata tantance wanne bane. Dan uwanta ahmad dai?,ahmad da aketa fadi wanda batayi wayon da zata ganeshi ba a sanda ya bace?. Amma wannan fuskar kamar tana mata kama da wata fuskar.......duk da ta rasa ganowa inda ta taba ganinta,koma a inane tasan bataga fuskar da yawa bane da babu abinda zai hanata tunawa. A hankali ya qaraso gaban sultane,sultane din dake zaune saman doguwar kujera shi da akhnan da falaak da suke zaune dama da hagunsa. Sulalewa yayi saman gwiwarsa cikin tsananin girmamawa yana soma gaidashi da yaren Tuareg,abinda ya saka tsananin farinciki a zuciyar sultane,don bai taba tunani ko kawowa zaiji yaren ba. Daga gaban sultane sai ya isa gaban manyan da suke nan gaba daya ya fara gaidasu,suna girmamashi yana girmamasu,yanayin daya sanya taruwar qwalla cikin idanunsa. Ashe wannan shine tushensa?,ashe wannan shine asalinsa?,ashe wannan ne dalilin da yasa kullum kuma kowacce rana yakeji a ransa rayuwarsa ba tasa bace?,ashe shi yasa yaqi gamsuwa rayuwar da yake gudanarwa itace rayuwarsa?. Komawa yayi ya gaida yakumbo nannie da morsa data iya amsawa da qyar saboda kuka,sanda ya iso kan mammina ji yayi zazzafan mari ya kamata ya sauke mata ba gaisuwa ba,amma koda tuna da kalaman haisam sai ya basarwa yana gaidata da wani irin yanayi daya sanya gabanta tsananta faduwa. Irin kallon da take gani a idanunsa suna tabbatar mata da gaske almaz dinne,irin kallon da take gani tattare dashi yana gaya mata cikin hayyacinsa yake......cikin kuma hankalinsa yake. Ba wani abu daga tunaninsa daya bace.....ba wani abu daga tunaninsa daya sauya ko ya samu naqasu. "Almaz ne" Ya fada yana kallon tsakiyar idanunta bayan ya miqe da sautin da ba wanda yaji daga shi sai ita. Wani abu taji ya daki qirjinta......abun daya taho da tsananin qarfinsa ya kuma dunqule mata a qirjin ya sanyata jin jiri tana daga zaunen,sai gashi ta gagara zama tana neman sulalewa. Nannie ce ta tarota tana salati,wani irin numfashi mamminan ke fiddawa gumi kuma yana yanko mata saboda yadda take kokawa da numfashin nata,da alama iskar gurin bata isarta. "Akwai taimakon da za'a bata?" Sultane ya fadi yana duban haisam adan rude,kai haisam ya gyada,sannan a nutse yace. "Daki kawai za'a kaita.....sannan a kunna mata wadatacciyar iska a bata guri ita kadai". Da sauri sultane yasa aka kira tafisu da sauran manyan hadimanta suka dauketa bayan sultane ya taka har zuwa bakin dakin taron. "Yanzu zamu kammala zaman,idan akwai wani rashin ci gaba a yanayinta a kira likita kafin mu fito" Ya fadi sannan ya juyo yana dawowa ciki. Dukkanin takardun gwaje gwajen qwayar halitta nashi dana ahmad DNA test ya gabatar musu,bawai kuma don kowa bai yarda ba,aah saboda sake samun tabbaci da nutsuwar zuciya. Duk wanda yake zaune a gurin girmama lamarin ubangiji yakeyi,sunata juya abun tare da taya sultane murna. Saidai ba wanda yasan ta yadda ahmad ya bayyana.....ko ta yaya aka ganshi,duk da kowa akwai wadannan tambayoyin a ransa,amma rashin bayyanarwa ya sanya ba wanda ya nemi ba'asin jin hakan. Wazeer,babban alqali na jaha,wali,galadima,shugaban limamai,da shugaban malamai dama ahalin diory hammani sunka wuce bisa rakiyar sultane gami da sake yiwa junansu barka da arziqin dawowar ahmad din cikin ahalinsa,sai dakin ya kasance daga sultane falaak da akhnan,sai morsa safiyya da nannie. Sai haisam dake zaune cikin kujera. Ya motsa zai fita tun sanda tsohon mamman hamza zai tafi amma sultane yace ya zauna. Akwai maganganu da yawa daya gani tattare da tsohon,wanda basu taba haduwa shi dashi ba sai a ranar. "Gobe hammud inason ganinka,kai da abokin takarata daya kayar dani" Ya fada yana duban haisam. Koda wasan kaka da jika yasha banban a ayaren Oromo da yaren Tuareg amma ya fahimci tsokanarsa yake,sai yayi murmushi sultane yana fadin. "Zanzo da kaina....zamu riskeka gida in sha Allah". Ko a yanzun yana zaune cikin kujera,waya ce a hannunsa yana sake tattara wasu bayanai. Idanunsa basa kan kowa amma cikin jikinsa yakejin Kamar akwai wasu idanu a kansa. Zaifi so sultane ya sallameshi don gurin ya sake zama na ahali sosai wato yasu yasu. Tsakanin ahmad da haisam batasan sau nawa ta raba idanunta a kansu ba. A duk sanda ta kalli ahmad din,sai ta dinga ji wani yanayi yana shigarta. Kaifi da qarfin jini.....wani yanayi na yau itama tana da yaya?,tana da wani jigo namiji dan uwa?. Idan ta kalli haisam sai taga bataga komai ba,bata hangi komai ba sai wani basarwa da shariya daga gareshi. Tunda ya shigo ba zata iya tuna ko sau daya da taga ya daga kai ya kalleta ba. Har gwara falaak data gaidashi taga yayi kamar ya kalli sashen da take yana amsa mata da wannan kamewar tasa. Ta sake zare dubanta daga kansa a hankali "Meye alaqarsa da bayyanar ahmad?......mene alaqarsa da nemoshi?" Ta tambayi kanta kokwanton data kasa warwarewa kanta shi. Daga idanunta ta sakeyi tana saukewa akan ahmad dake tsugunne gabansu ita da falaak. *zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 08187255862 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 08187255862 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 15* "Ni sunana ahmad,kefa kefa?" Ya fada yana dubansu dukka su biyun. Murmushi ya kubcewa falaak sosai da yafi kama da qaramar dariya. "Yaya ahmad.......ni sunana falaak.....ita kuma khadeeja,akhnan ko biftu,daa itace babba,amma yanzu tunda ka dawo kaine babban" Saida sukayi murmushi dukkansu harda ahmad din. Ya maida dubansa akan akhnan,har yanzu batayi magana ba. Da gaske dai haka dabi'arta take.....haka yanayinta yake,ba wani abu bane daban da a baya ya dauka. Ya hadiye wani yawu mai tauri da quna......ya dinga maimaita furta. "Alhamdulillah" Da tuni qanwarsa yake aure?,da tuni zuwa yanzu alaqa da mu'amala tsakaninsu tayi nisa?. Da mummunan nufin wancan shaidaniyar ya cika da yanzu me kenan?. Hannunsa ya miqa musu dukka sun biyun son suyi musabaha,sai falaak ta dora nata akai,amma akhnan saita noqe. "Ehemmm......ko har yanzu ban shiga cikin ahali ba?" Ya tambayi akhnan yana dubanta. A hankali ta sauke idanunta akan hannun nasa,wani abu ya narka zuciyarta sosai tashin farko. Yatsun sultane take gane a nasa hannun,tsahonsu da yanayin zubinsu,hatta da girman babban yatsansa na sultane ne,sai ta miqa masa nata hannun a hankali dukka ya hadesu guri guda nashi dana falaak da akhnan din. "Duk da zaku tafi a sanda ni nazo,ina fatan zan zame muku kamar sultane ko?,babban yaya naji kuna cewa shine madadin uba" Wani sanyi taji yana ratsa zuciyarta a hankali. A baya inda yana nan?,inda yana rayuwar ta qila shine zai dinga bata shawara?,shine zata dinga kaiwa kokenta?,shine zai duba daidai daba daidai ba qilan sama da yadda sultane yayi?. Idanunsa basa kansu,amna kunnuwansa suna gurin,musamman sanda ya isa gabansu......musamman sanda ta sanya hannunta cikin nasa sai yaji wani abu ya masa tsaye a wuya. Halal ce......ba haramun ba,dan uwnata ne na jini,uwa daya uba daya,to amma haka kawai wani wutar kishi ta d'isa saman ransa. "Na tsaidaka muhammad.......bari na barka haka sai gobe?" Sultane ya fadi wani girma yana fita daga idanunsa zuwa ga haisam. Wata irin qaunar haisam din yakeji sama da yadda yakejin ta yaransa,bai sani ba ko a nan gaba zai qaunaci ahmad kamar irin haka ko sama da haka?. Miqewa yayi fuskarsa adan sake,yana bawa sultane hannu sannan ya juya a nutse ya fara takawa don ficewa daga gurin. "Biftu......tashi ki bishi" Morsa safiyya ta furta da muryarta data dakushe kadan saboda kukan dazu. Tana ankare da ita......kamar bata gaidashi ba,hakanan bata bashi attention din daya dace ta bashi ba. Tana tsoron yadda akhnan din zatayi zaman aure......irin zaman auren nan da ake cewa iya zama ya sanya mace ta kame zuciyar mijinta. Ta sani akwai tarin naqasu dama gyare gyare,amma abinda yake bata nutsuwa da kwanciyar hankali nau'in mijin data aura din. A hankali take takawa,iskar da tun da yamma bata yankewa duniya ba tana ci gaba da kadawa cakude da qamshin qasa da kuma sanyin da hadarin ya bari,saidai sanyin ya yiwa halittu da dama dadi,saboda baiyi yawa sosai ba saima wani shiga jiki da yake yana sanyayar da zukata. Kamar yadda hanyar take a baya,shuru don ba hanyar shigar kowa bace.....shimfide interlock da bishiyoyi hagu da dama dake sake bawa gurin yanayi me kyau. Duk taku daya sai taji zuciyarta ta buga kafin a hankali ta soma jiyo wannan mayataccen qamshin. Cak ta tsaya,don idanuwanta dai basu gano mata shi ba,a hankali ta soma juyawa zuwa bayanta zuciyarta na wani motsawa da wani irin yanayi. Yana tsaye tsaf daga bayanta. Dukkanin hannuwansa cikin aljihun kuftar jikinsa. Lafiyayyen tsadajjen yadin kuftar da aka yiwa aikin sarauta wuya da hannu da bakin aljihu qasan wando harma da gefe da gefan rigar. Yayi wani irin sassanyan kyau.....karon farko data ganshi cikin shigar da bata taba ganinsa da ita ba. Shigar ta wani amsheshi,tabi jikinsa.....zaka dauka ya hada jini da al'ummar nigeria......qasar hausa,bakano wanda cikin jerin jinsin mazan da sukafi mazan kowanne gari sanin haqqin wanka,saidai kuma kash.....wannan sassalkan gashin nasa dake kwance saman kansa.......wannan zubin nasa daya banbanta da qira da siffar kanawa ko qasar nigeria......shine abu daya da zai gaya maka wani qabila ne daban da bahaushe ba. Inda zata iya buda baki tayi magana,abinda zatace masa shine. "Kaci gaba da saka irin wadannan kayan.....suma sunayi maka kyau kamar yadda cloak thobe ke maka" Saidai bugawar da zuciyarta keyi ma bazai bari komai ya fita a bakinta ba. Tana jin nauyin idanunsa a kanta sosai.....suna mata wani irin tasiri da taji kaman tana son daburcewa,ta rasa wanne irin idanu ya mallaka masu kaifi da kwarjini har haka?. Wani abu yake gani cikin idanunta,wani abu da yaja ra'ayinsa kadan,ya sanyashi sake cusa hannuwansa a aljihun rigarsa. Kansa ya karkatar kadan yanason lalubo qwayar idanunta,amma kuma ya gaza yin hakan sam saboda yadda taqi daga fuskarta da kyau. Ya kafeta da idanu....baice mata komai ba......bai kuma bata hanya ba,hakanan ya daureta sosai da wannan idanun nasa masu tsananin kwarjini. Daburcewa ta soma ji sosai cikin jikinta......ta soma complain ita daya qasan ranta. "Yasan kaifin idanunsa akan dan adam kuwa?" Ta tambayi kanta da kanta,tambayar da babu abinda ta qara mata sai rudewa. Can qasan ranta kuma har yanzu da wannan feeling din,kwana biyar yayi maimakon hudu,a kwana biyar din bai nemi koda wayarta ba,bayan sun hadu kuma by incident sai ya sake bace mata?. Sai a yanzu ta ganshi a gaban kowa?. Kuma ko bayan ya gama zamanshi bataga ya kalli koda inda take ba?,hasalima sai ita aka yiwa tayin binsa?. "Kaman girmana ya tabu" Taji can qasan ranta wata zuciyar tana gaya mata,hakan yasan ranta yadan tabu kadan. "Ko zan iya komawa?" Ta fada da muryar nan tata me wani irin laushi. (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) Iska sosai yaja,wata irin iska data zuqo masa dukkan qamshin dake fita a sanyaye tun daga gashin kanta zuwa sassan jikinta. Ya fesar da iskar a hankali yana lumshe idanunsa gami da budesu. Yadda take avoiding kallonshi tun a wancan ranar.....akwai wani abu cikin idanunta da yake karantarsa tas. Yana da wannan baiwar......baiwar iya karantar dan adam da tunaninsa ta cikin ido. Sosai take sake jin yana aza mata nauyi,tana jin kamar ta daga idanunta ta kalleshi......kamar ta daga kanta taga meye ya tsaidashi?......bai amsa mata ba,kuma bai tafi ba,bai kuma barta ta samu daman tafiya ba. Tarin da taji yadan fara yi kaman ya qwarene ya sakata daga kanta da sauri,saurin daya haifar da shigar qwayar idanunta cikin nasa,fuskarta a dan yamutse da alamun tsoro na tarin daya sarqeshi,saidai suna hada idanun saita sameshi qyam a tsaye,ba wani alamun jigata ko kuma sarqewar tarin kamar yadda taji sautin. Wani irin riqe qwayar idanunta yayi cikin nasa. Sosai ya nutsa qwayar idanunsa cikin nata,ya lumshesu sau uku yana budesu duka cikin nata da wani irin yanayi na qwarewa wajen sarrafa dan adam ta cikin idanuwa kadai. "Duka fushin na meye?" Ya furta da wani irin soft and cool voice,ba taushi da sanyin muryar ba kawai.......can cikin sound dinsa akwai wani irin deep abu dake ajiye magana sosai cikin kunnuwa da qirjin me sauraro. Ji tayi kaman qafafunta suna lanqwashewa,kallon yayi mata nauyi da zurfi da yawa,inda ace tana kusa da wani abunne tabbas da zai taimaka mata qwarai,don zata dafashi don ta samu daidaito gurin tsaiwa. "Ehmmmm?" Ya fada still yana hana idanunta motsawa daga cikin nasa. Kallon kallo ne ya sake wanzuwa tsakaninsu,kallon da ita daya tasan me yake ajiye mata a gangar jikinta da zuciyarta,sawa yake kowacce gaba ta jikinta tana laushi. "Akhnan ce fa?,princess akhnan" Wani sashe na zuciyarta ya tunasar da ita. Wannan shine ya bata wani qwarin gwiwa,qwarin gwiwar zame idanunta sannan taja da baya kafin ta juya da nufin saka nisan tazara tsakaninsu. Saidai kuma kyawawan taku uku kawai ya cike tazarar,ya kuma sha gabanta da kyau,har yana mamaye tsahonta gaba daya,yana kuma lullubeta da faffadan kafada da qirjinsa. Haka kawai sassanyan qamshinta ya masa....haka kawai yaji kaman yayi sauri ace ta koma ciki yanzu.....kamar akwai ragowar mintuna.....kamar akwai abinda yakeson ya fada. "Gaisuwa.......gaisuwa sai ance kiyi?" Ya fadi yana dubanta har yanzun. "Barka da dare" Ta samu kanta da hanzarin fada. Ba don maganansa ba,sai don tana buqatar ya tallafeta ya bata hanya kafin ta gagara mallakar kanta. Koda wasa bata bari ta sake kallonsa ba,hanya kawai take nema,bata kuma ganta ba muddin bai matsa mata hanya ba. A hankali ya sauke idanunta kan yatsunta,karo na farko daya sake ganinsu a zahiri ba a allon computer ba irin jiya. Sosai ya zube musu idanunsa. Ya sani,tun ranar daya karanta cikar sunna ga jan lalle,umarnin ma'aiki ga mata dasu zama masuyin lalle,tun daga wannan rana son abun ya shiga ransa,musamman daya tashi ya samu Nanay dinsa ma'abociyar yinsa ce,ta kuma koyawa kowa cikinsu rumaisa Anaani noorah yinsu,hatta da khansaa'u dake gidan aure. Motsa yatsun tayi kadan,kamar tasan su yake kalla,hakan sai ya sake daukan hankalinsa,yabi yatsun da kallo yana jin kamar ya miqa hannu ya shafa yaji yaya suke?,yaya lallen yake a hannunta?. "Zan iya samun hanya?" Ta sake fada still ba tare data kalleshi ba. A hankali ya janye gefe yana bata isashiyar hanyar da zata wuce din. Ta qasa......ta qasan da idanunta ke zube saman rufaffun takalman qafarsa taga yaja bayan,wani abune yayi mata tsaye a rai,don tace zata tafi?,sai kawai ya bata hanya ta sauqi irin haka?. "Kina lafiya?,ba wani matsala?" Ya sake fadi da muryar da tafi ta dazu laushi. Kai kawai ta gyada masa a hankali taci gaba takawa tana wucewa. Baisan me ya tsaidashi a gurin ba,yaci gaba da bin takunta da kallo,abinda a yau karon farko ya fara noticing. Wani irin cat walking,kowacce qafa kaman akwai qa'dar ajiyeta. *zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 08187255862 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 08187255862 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 16* *_A K H N A N_* Tun daga wankanta zuwa kammala shirin baccinta komai ne yake dawo mata cikin kanta daki daki. Wannan kusancin......wannan kallon......wannan qamshin nasa da yake sake mannewa cikin zuciyarta da rayuwarta gaba daya. "Me yasa yake da izza har haka?" Ta sake nanata tambayar da har yanzu ta gagara samun amsarta. Tunda take a rayuwarta,ba zata iya tuna wani namiji da izza ke nunawa cikin komai nasa ba irin haisam din,haka malaman suke?,ko kuma daga shi dinne?. Sake qanqame jikinta tayi guri guda gami da cusa pillow tsakanin qirjinta kamar zata maidashi cikinta. "Me yasa yake saurin surrender?......me yasa idan nace abu baya kafewa akai?" Ta sake tambayar kanta tana jin wani rashin dadi. Kaman dazu,ta dauka zaice ba zata tafi ba,ta dauka zai gaya mata uzurinsa na qarin kwanakin da yayi akan wadanda yace zayayi din,amma babu ko daya a ciki. Hasalima sai daga qarshen qarshe yake tambayarta lafiyarta......wannan shine MIJIN?. Tambayar data yiwa kanta na qarshe ya karyar mata da zuciya,sai taji wani dumi cikin idanunta kamar hawaye yana son taruwa. Ta lura da sauye sauye kan komai na sassanta,kama daga cima,yanayin tsaro da sauransu,koda bata tambaya ba tasan daga shine.......amma kuma sai taji duka kamar wannan bai gamsar ba. "Me yasa kike damuwa.....miji ne fa kawai da aka aura miki ba amincewarki" Wani sashe na zuciyarta ya rada mata hakan a hankali,abinda ya sanyata ware dukkanin idanunta tana kallon bangon dakinta duk da duhun daya mamayeshi,kamar meson tuna wani abun na daban. Kuma kamar jira akeyi tayi hakan wayarta dake silent ta fara haske. Idanu ta zubawa wayar,zuciyarta na bugawa a hankali a hankali. Haka kawai takejin wani fata yana shigarta game da kiran wayar......haka kurum take raya wani abu kan kiran daya shigo mata wayar a daidai wannan lokacin,wannan fatan da saka ran ya sanya ta miqa hannunta da hanzari tana daukan wayar,saidai kuma sunan aisa ta gani baro baro saman wayar. Mamaki kadan ya kamata........tadan ware idanunta,aisa a irin wannan lokacin?. Ta sani sam ba dabi'arta bace kira late da dare haka,idanma zata nemeta irin haka inde dare yayi saidai ta shaidawa barratu ko birra su sanar da ita ta duba watsapp dinta. Dab da kiran zai katse ta dauka,ta saka wayar a kunnenta ba tare da tace komai ba. "Biftu" Taji muryar aisa da tayi wani irin mugun sanyi ta kira sunanta. "Aisa?" Ta maimaita sunanta itama tana jin wani yanayi. "Kiyi haquri biftu.....na kasa.....na gaza riqe wannan amanar,komai yafi qarfina biftu bazan iya ba,zan ajiye zan dawo agadez" Tayi maganan muryarta wani iri. Shuru akhnan tayi,zuciyarta na faffasa yadda taji sautin muryar aisa. Muryar aisa ba haka take ba.....ba haka yanayin aisa yake ba,bata da wannan raunin,tana da taurin zuciya da kafiya shigen nata,duk da cewa ita ta fita sauqin sarrafuwa da sassauci. "Mene ne aisa?" "Komai ma biftu,komai ma,amma kiyi haquri ki yafemin,zanzo zamu zauna,komai nawa yana gayamin KIN GAZA AISA.....komai nawa yana gayamin kaman naci amanarki ne,kamar ban kyauta ba,kamar zunubina bazai wanku ba,kamar na zama sanadi.....kamar nice sila" Dukka tayi maganan muryarta tana sake raunana sosai. Maganganun sunwa akhnan nauyi da girma da yawa,tana qoqarin magana taji alamun aisa ta datse kiran,ta kalli screen din,saita soma yunqurin kiranta amma na'ura ta shaida mata wayar a kashe take gaba daya. Bata natsu ba,ta miqe ta zauna ta fara kiran shehnaz. Kaman dama wayar na hannunta ne tana jiran kiran akhnan din ta daga. "Shehi....Qu'est-ce qui se passe avec Aïsa?(me yake faruwa da aisa?" Ta tambayeta da french. "Je ne sais pas.mmmmc'est étrange,je me demande pourquoi elle pleaurait(Ban sani ba nima,baqon abune wannan.....inata mamakin me yasata kuka)" Ta fada da alamun damuwa sosai cikin muryar shehnaz din. Shuru akhnan tayi,tana sauraren bayanan shehnaz. "Tun kwanakin can nake jin yanayinta kamar ba'a daidai ba,bata fadamin ba bata kuma nuna tanaso naji ba shi yasa ban matsa mata ba,amma koma meye gobe ko jibi tace zata taho,ko bata sameki ba ni zan jirata naji" Kai ta gyada a hankali "Allah ya kaimu". Ta katse wayar sannan ta koma a hankali ta kwanta,saidai har zuwa sanda bacci ya dauketa aisa ce a ranta. *M A M M I N A* Bata taba jin tana so tayi kuka a rayuwarta ba irin yau........ta jima kuma bataji kuka yana neman hallaka numfashinta ba irin yau din. Duk wani hadimi da hadima dake kusa kusa da dakunan baccinta ta sallamesu,ta kuma kulle kanta a daki tayi wani irin kuka harda ihu daidai da yadda take jin baqincikinta zai ragu. Batasan adadin tsahon lokutan data dauka ba a haka ba,har sai data tabbatar ta samu sassaucin abinda takeji qasan ranta,sannan ta shiga bandaki tayi wanka da ruwan sanyi waiko zata samu sassaucin abinda takeji cikin jikinta. Dawowa tayi dakin,tayi zaman dirshan,zaman 'yan bori tana qoqarin farfasa tunaninta daya bayan daya. Ayau,ta samu dukkan tabbaci da yaqinin sheikh muhammad haisam yana cikin jerin sahun mutanen da suka shigo agadez don farmakarta "Idan ba haka bane?,me ya hadashi da almaz?......kenan dama can almaz din yana hannunsa?,idan haka ne dukka al'ummar villa street suna hannunsa kenan". Wani irin zazzafan gumi taji ya karyo mata,haka kawai takejinta kamar ita kadai ce.....haka kawai takeji kamar ita kadai ta rage a wannan sansanin,......a wannan filin. Batasan me yake damun tafsu ba,cikin kwanaki gaba daya wani nesa takeyi da ita wanda ta bada uzuri da juyawar ciki da har yanzu ta kasa saurara mata. Da waye zatayi shawara?,waye zai hango wata mafitar da ba lallai ita din ta hangota ba?. (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) Tambayar da tayi mata tsaiwar mashi aka,bata kuma samo amsarta ba......sai wani courage daban da takeji daga wani sashe na zuciyarta. "Karki yadda ki fadi.....karki yadda kaikai qasa......koda yanzu kina tunani motsinki zai iya zama barazana.......ki bashi lokaci,sanda zai tashi daga agadez zuwa qasarsa......wannan futar ki tabbatar ta zame masa fita ta qarshe daga qasar......daga yankin nan. Fitar da zata sama nisa na har abada tsakaninsa da agadez da kuma sultane. "Ki daure......a qarasa komai dashi......ya fita yabar qasar,komai zaizo da sauqi" Wani murmushi ta saki,murmushin dake da alaqa da sassaucin data samu da 'yan qanqanuwar mafitar da zuciyarta ta bata. Burinta a yanzu ba control bane......babban burinta a yanzu shine ta qarasa aikinta na ture kaza daga kan qwai ta kwashe qwan.....kauda sultane me gaba daya,ta kuma tumbuke bishiya daga tushenta,tayi rantsuwa........ta kuma lashi takobin tabbatar da wannan aikin,a kusa ko kuma a nesa. Wayarta dake gefe ta dauki qara da tsuwwa,ta waiwaya ta zuba mata ido kamar ma ta manta da ita. Kamar ta shareta,kaman kada ta dauka,amma sai sunan dake harbawa saman screen din yaja hankalinta,ta miqa hannu ya daga ta saka a kunne. Batace komai ba,amma maganan da ake mata daga wancan bangaren ya sanya wani shu'umin murmushi subuce mata. "Ko a iya nan kun kammala aikinku......inaso kowacce hujja ta bata ta salwanta kamar komai bai taba faruwa ba.....burina akan sahel couture ya gama cika........aiki ya kammala.......ku jira sakamakonku........ina alfahari dakai" Takai qarshe tana cije labbanta da haqorinta irin na zallar muguntar nan,sannan ta zare wayar a kunnenta har yanzu murmushi yana sauka saman fuskarta. "Kafin na tafi......ya kamata kowa ma ace anbar masa wani babban tabo.....babbar barakar da bazata taba gyaruwa ba" Ta fada a bayyane tana jin alamun nasara na tare da ita kena,tunda har a sanda take zaton faduwa babban labarin nasara yazo mata. *_RANA BATA QARYA_* Cikin wani irin tarin nutsuwa yake zaune gaban sultane,wanda ya kebe ne daga shi saishi,duk da cewa shi da maleek ya fara yin magana dasu. Sanye yake cikin wata qayatacciyar jallabiyya da asalin kudinta ita da cloak thobe din jikinsa yake isa babban jari da tarin al'umma marasa qarfi. Wasu irin thobe da a idanu kawai idan ka kallesu kasan an nunawa kudi iyakarsa wajen mallakarsu. "Na aura maka biftu ne......saboda fadin manzan Allah.......mu aurar da diyoyinmu ga maza irinka,idan ka sota zaka mutuntata ka mutunta ahalinta,idan ka qyamaceta kuma ba zaka wulaqantata ba........haisam,bazan boye maka ba,ba kuma don ban aminta dakai ba aah......ina sake jaddada maka ne kaji tsoron Allah akan khadeeja.....bazan boye maka ba,inason khadeeja sama da kowa cikin 'ya'yana.....amma hakan........" Sai zuciyar sultane dake kashingide saboda rashin qwarin jiki da yake fama dashi ta raunana. Ya yunqura ya miqe ya kuma zauna sosai,rabon da yaji alamun taruwar hawaye cikin idanunsa tun rasuwar mahaifiyarsa. "Amma hakan bazai hana na aurar da ita ba,saboda hakan shine cikar kamalar mace.........ina sake baka amanarta......ba don ina kokwanto kan cikar kamalarka ba,a yanzun duk duniya,ba wani d'an adam dana aminta dashi sama dakai" Wani irin nauyi yakeji sultane yana sake aza masa.......wani irin sanyi dukka yake ji yana bin jikinsa. Yana jin kamar bazai iya ba.....kamar bazai kai labari ba. Ya sani,idan ana maganar amana wata abace me girman gaske......abace da idan ba ita tsallake siradi kansa baya yiwuwa a gurin bawa. Zata kasance abu mafi santsi a tafin hannun bawa ranar qiyama,ita zaa aza maka a hannunka ka tsallake wannan siririn zaren da ko kaurin gashi baikai ba.....siririn zaren dake tsakanin wutar jahannama,ka tsallaketa da ita,tana santsi kamar tarwada a hannunka. Duk sanda ta subuce ta fada to zaka bita ne ka daukota don ba zaka wuce ba sai da ita,idan kaci amana zaka yita sintirin daukota daga wuta Allah ya tsaremu,idan kuwa ka kiyayeta lafiya qalau shikenan zaka wuce,wucewar da babu wani bawa da yake da tabbas a kanta. (Ya Allah,ka bamu ikon kiyaye amana....Allah ka tsallakar damu siradi lafiya). "Muhammad" Sultane ya kira sunan haisam da yanayin daya sanyashi daga manyan idanunsa kadan ya kalleshi. "Akwai wasu abubuwa a wancan ranar dana gani......akwai abubuwa da yawa dana saka musu ayar tambaya.....akwai abubuwa masu yawan gaske daya kamata ace na sani inaji a jikina hakanan......inason nasan gaskiya muhammad......inaji a jikina akwai wani boyayyen abu......shin zaka iya riqo da hannayena na sauka daga mulkina na damqawa ahmad?......zaka iya dafawa raunina ka fiddani daga cikin duhu zuwa haske?" Maganan ta zowa haisam a bazata,magana data sake tilastashi daga kansa a hankali yana duban sultane,yana masa wani kallo ne dake bayyana gaskiyar magana manufa da abinda yake fadi daga tsakiyar zuciyarsa ne *zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 08187255862 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 08187255862 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 17* *M O R S A S A F I Y Y A* Zaune suka a gabanta dukka su biyun,sanye kowaccensu da abaya data banbamta gurin launi da design din ma gaba daya. Falaaq na sanye da dark mint green,wadda aka saqata da ainihin satin material me kyau da tsada. Yayin da akhnan ke sanye da baqar abaya,Japanese nida da aka saqata daga asalin yadin silk me yauqi dake shaking yana sake qawata farar fatarta dama ainihin kalar baqi wul din da abayar ke dashi. Zaune suke gaban morsa safiyya,a kebantaccen dakin kwananta da babu kowa a cikinsa,daga ita sai 'ya'yan nata guda biyu. Dukkaninsu tafukan hannuwansu suna cikin nata,na tsahon wani lokaci suka dauka a hakan,duk wani magana da zata musu koda kalma daya bata bari ta fadeta suna nesa da ita ba,ta damqesu sosai cikin nata hannuwan,tana jin kamar ba zata iya zame hannun nasu daga cikin nata ba. Wani emotion ne me nauyi tun daga idanunta zuwa zuciyarta,irin wannan yanayin da UWA data aurar da d'iyarta ne kawai ta sanshi a ranar da za'a karbe diyar daga hannunta zuwa gidan wani. Sheshsheqar kukan falaak ita ta haifar da wani irin shuru a tsakaninsu,wani irin shuru dake dauke da nauyin da zuciya ce kadai tasan iya adadin mizaninsa. Komai akhnan tana jinsa ne kamar almara,komai tana kallonsa ne kamar wani shirin film ko a littafi. Yau ita akhnan?,itace wani d'a namiji zai dauketa cancakat?,daga mahaifarta?,daga masarautarta?,daga cikin iyali da ahalin data taso a ciki?. Ba Niamey kawai zata bari ba.....ba agadez kawai zata bari ba.....aah,zatabar qasarta da nahiyarta ne gaba daya. Karon farko da taji kukan falaak ya sanya wani rauni cikin zuciyarta,lokaci na farko da riqon da morsa safiyya ta yiwa hannuwanta take jinsu har cikin qasusuwanta da zuciyarta. "Ya isa falaak.....ya isa ha...." Sai muryar morsa safiyya din ta maqale,salin alin kuma ta hadiye sauran maganganunta gudun kada hawaye ya balle mata,ta karya musu qwarin gwiwar da take musu tattalinta. "Momma......sultane fa" Muryar ahmad dake takowa cikin dakin ta sauka a kunnuwansu gaba daya. Murmushi ta qaqalo,ta soma qoqarin zame hannuwanta da take zaton falaak ce kawai zatayi gardama,saidai ga mamakinta tsam taji akhnan ta riqe yatsunta cikin nata. A hankali ta daga idanunta tana duban morsa safiyya din,sai a sannan taga damshin hawayen daya jiqa zara zaran eye lashes dinta. "Kiyi haquri" Akhnan din ta furta a hankali labbanta suna motsawa. Kai morsa safiyya ta soma girgiza mata,akwai tarin abubuwan data karanta tattare da ita,saidai a yanzun a wannan lokacin ba muhallinsu bane gaba daya. "Biftu" Ahmad ya fada a nutse yana tsugunnawa a tsakiyarsu yana sanya hannunsa cikin dabara yana raba tsakanin hannuwansu dana morsa safiyya "Ya isa.....muje sultane yana son ganinku" Ya fada da wani irin yanayi da yasa ba wadda ta masa musu a ciki,ya bude musu nashi tafin hannuwan suka saka hannunsu a ciki ya miqe tare dasu gaba daya. *_HAISAM/SULTANE_* "Ina kyautata maka zato fiye da yadda kake tunani" Sultane ya sake fadi bayan gajeran kallon kallon daya ratsa tsakaninsu shida sultane din. Sallamar ahmad itace ta katse ragowan dukka tattaunawar data rage tsakaninsu. "Wa'alaikumussalam" Sultane ya amsa sallamar murmushi yana subuce masa daga saman fuskarsa. Idanunsa akan ahmad din wanda ke riqe da hannuwan akhnan da falaak. Cikin girmamawa ya isa gaban sultane dasu,ya ajiye masa su,a daidai lokacin kuma haisam ya miqe a nutse ya taka yana fita daga dakin. Basai sultane ya fada masa ba,a yanzu a wannan lokacin,baya buqatar izinin sultane waje fita a gurin,lokaci ne na uba da 'ya'yansa,lokaci ne na ganawar mahaifi da yaransa cikin sirrin da su kadai ya shafa. "Allah yayi muku albarka,Allah ya albarkaci rayuwarku da aurenku gaba daya......bakuyimin komai ba tsahon zamanku tare dani,idanma kunyimin din na yafe......saidai kuma akwai abu guda daya da zaku iyayimin wanda ba lallai na iya yafeshi ba". Dukkaninsu......daga falaak har akhnan sai da suka daga kai a gigice suna dubansa. Da murmushi a fuskarsa yake jinjina kansa. "Eh,kuqi zaman aure,kuqi biyayya wa mazajenku......ku bijire musu,kuqi binsu cikin abinda Allah da manzonsa suka shard'anta....inde ba cutarwa ba zalunci ba tauye haqqi......ku zauna a gidajenku,kuyi biyayyawa mazajenku,wannan shine abu guda daya da nake buri,nake kuma buqata daga gareku" Ya qarasa fada da wani irin sanyi a muryarsa. "In sha Allah bappi.....in sha Allah zakayi alfahari damu" Falaak ta fada muryarta na rawa tana kama tafin hannun akhnan tana riqewa cikin nata,kamar tanason ta bata tabbacin maganan data gayawa sultane. "Allah yayi muku albarka,yasa aljanna ce makomarku" (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) "Ameen" Labban akhnan suka motsa da qyar ta amsa,kafin muryarta can qasa tace. "Bappi......ka yafemin" Kalmar ta fito tare da silalowar hawaye daga cikin idanunta. Murmushi ya sake saki,yana jin yadda jikinsa a kowacce rana yakeyin weak. "Kisa a ranki baki taba batamin ba akhnan......baki tabamin laifi ba......amma nan gaba zaki iya yimin matuqar baki tsaya kin yiwa Muhammad biyayya ba......a yanzu duk wani hasashe naki na ido bazai iya gaya miki waye muhammad haisam ba......amma zan fada miki wayeshi,qila a nan gaba idan kin tuna da kalmata koda bana raye zaki ga ta hau daidai da mizanin dana fada miki......muhammad haisam LU'U LU'U ne......LU'U LU'U n da ke lullube cikin wani guri da hankulan mutane da iyaye baikai kanshi ba.....amma hakan yayimin.....inda hankula sunkai kansa da wurwuri.......qila a yau da banyi nasarar zama surukinsa kamar haka ba" Ya qarasa fadar maganan murmushi yana balle masa. Dukkan alamunsa sun nuna sosai yakejin dadin yanayin......sosai abun yake masa dadi har qasan zuciyarsa. "Ko bayan bana raye....ko bayan na mutu ki tuna wannan" Kalmar mutuwar daya ambata saita zame mata kaman wani babban abun barazana daya birkitata,ya kuma sanyata fashewa da kukan da tun dazu take neman control dinshi dama,ta fada jikin sultane ta riqeshi da kyau kaman ba gobe. "Ba zaka mutu ba bappi na......ba zaka mutu ba......zan fasa tafiya na zauna da kai" Riqeta yayi sosai yana share mata hawayen da hannuwansa,Shima tana sake kashe masa zuciya da gangar jiki bayan kasalar dake sake mamayarsa a kowacce rana. "Kin manta na fada miki farinciki na?,......farincikina shine zamanki gidan aurenki,kibi umarnin mijinki ki samu aljanna khadeejatu" Kusan a cike farfajiyar gidan take da jama'an da suke da kusanci da ahalin sultane muhammad hammud,yan uwa bayi da hadimai da suka zama tamkar 'yan uwa na jini ga iyalin me martaba. Motoci ne na alfarma guda goma aka ware don tafiya daga agadez zuwa Niamey,cike da hadimai da zasuyi masu rakiya har zuwa sanda zasu tashi daha babban filin sauka da tashin jiragen sama na Niamey Diori hamani international airport,wanda daga can suka tsara yadda zasu tashi zuwa jedda Sultane ne da kansa riqe da hannuwansu yana takawa ta jerin mutanen dake tsaitsayi hagu da dama suna bankwana dasu cikin nuna kulawa da soyayyar da ta samo asali daga adalin mahaifinsu. Haisam da maleek din dukkaninsu suna bayan sultane din,cikin kamala da shigar dake sake nuna zallar haibarsu. Motocinsu ya banbanta,kamar yadda sultane ya sanya kowacce cikin motar da aka tanada don tafiya da ita ita da mijinta. Janyewar sultane baya ya soma takawa don barin gurin gudun tsinkewar zuciya shi ya bawa mammina daman matsowa. Cikin wannan shigar dake nuna alfahari fariya da izzarta.....cikin suturar da kowanne lokaci take zabar mafi qyalqyali da jan hankalin sutura don nuna tarin girman isarta. Idanunta cak saman fuskar haisam......saman fuskar haisam din da ko sashen da take bai kalla ba,hasalima ya maida hankalinsa wajen tura saqo ga dukka ayarin ta hanyar na'urar dake cikin wayarsa na cewa airport din agadez zasu nufa maimakon bin kwalta zuwa Niamey kamar yadda aka shirya da farko. "Yata......ba shakka zanyi kewarki......irin kewar da ban taba irinta ba,banda aure ba wani abu da zai iya yimin wannan yankar qaunar tsakanina dake,saidai na godewa Allah daya sanya komai zai zamana na gajeran lokaci ne........kada wani yanayi ya rudeki ki manta da mafarkanki......jajirtacciyar mace bata yin barcin da zai kaita ga mantawa da mafarkanta dama burikanta........ka tsaya tsayin daka,ka gina mafarkinka......ka gina burinka......karka bari wannan mafarkin ya rushe.....wannan shine cikar jajirtacciyar mace........kina da dama.....kina da fili.....kina da gurbi.....kuma kina da sarari na gina mafarkanki,koda hakan yana nufin zaki canza hanya da mutane masu yawa". Tayi maganan tana runtse hannunta cikin na akhnan. Haka kawai akhnan takejin bataji wannan kewar ba......haka kawai takejin bataji wannan yanayin ba da taji a tare da morsa safiyya sanda hannunta yake cikin nata. Ba komai da takeji illa burin zame hannunta cikin nata,haduwar hannuwansu guri guda baya tuna mata da komai sai alqawuranta......wadannan alqawuran da sukaso rudar da ita.....suka jefata wani mummunan yanayin da har yanzu bata da tabbacin ta fita ko tana ciki?. Banda nutsuwar da take samu a yanzun batasan wanne suna zata kira kanta ba,batasan wanne suna zata kira rayuwarta dama dukka sauran burikanta ba. "Sheikh muhammad haisam" Ta kira sunan haisam kai tsaye. A nutse cikin wani irin yanayi da kallon dake dauke da ma'anar BAKI DA MUHIMMANCI ya zube idanuwa fes saman fuskar mammina din. Fuskar daya tabbatar shi yaga dama ya barta har zuwa yanzu......harma takejin tana da zarra da qarfin halin furta wadannan kalaman.......amma ya tabbatar yayi imani abinda ya tanadar mata saita gwammace bata taba walqawa cikin rayuwarsa shi muhammad haisam ba. *zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 08187255862 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 08187255862 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 18* "Ina fatan dai ka sani.....duk da cewa komai temporary ne......buzuwar mace......tana da cikakken 'yanci,mata ne masu 'yanci,masu son 'yanci.....masuson walwala da barinsu suyi rayuwarsu cikin sakewa,basusan wahala ba ko wasu dokoki da zasu taqaita musu jin dadinsu ko walwalarsu ba.....saboda haka nake cewa,ka kula da ajiyarmu zuwa lokacin da zamu karba.........inaso kayiwa agadez kallon qarshe....don ba lallai ka sake samun dama kwatankwacin wannan a rayuwarka har abada" Ta qarashe maganar da wani irin kallo cikin idanunta. Nasa kallon ya zurfafa a kanta,kallon da duka duka na sakanni biyar ne,saidai qasa da second biyar din wani abu me qarfin gaske ya nemi rusunar da nata kaifin ganin. Abu na qarshe daya daketa sosai har cikin jijiyoyinta murmushi ne.....murmushi daga fuskar haisam......murmushin da bata buqatar fashin baqi ko qarin bayani daga gurin kowa. Da baya take ja a hankali amma idanunta suna kan motocin da suka fara hawa saiti don fita daga masarautar.....motar dake dauke da lamba shidda casss.....motar da haisam da akhnan suke ciki,motar da takejin tana dauke wasu abubuwa da suke da nauyi a mizanin Rayuwarta. Saidai kuma murmushi ya subuce mata,murmushi ya kubce mata saboda hangen nasara......samun sarari da kuma samun cikakkiyar dama na sarrafa SULTANE da masarauta gaba daya. Saidai wani abu guda da bata sani ba......sanda take kwance a lokacin haisam ya tsere mata da wani irin matakin nisa a gudu......sanda take fara tunani......a sannan haisam ya kammala nasa har ma ya rufe babin yana jiran chapter ta gaba. Sanda motocinsu ke kammala fita daga gidan......sanda ta juya tana komawa ciki cikin murmushin nasara......a daidai wannan lokacin 'yan press(yan jarida) motarsu ke kutso kai,daga babban gidan tv da radio na qasa. *_Tofa.......😄,me kuma zai faru?_* Wani irin shuru ne ya ziyarci cikin motar,shurun da haisam yayishine yana qoqarin controlling fushinsa. A yanzu babu muhallin yin fushi,sarari ne da fara shimfida girbi bayan baqar shukar da aka dade ana yinta. Shurunsa yana zarcewa ne da maimaita kalaman zaituna cikin kansa. Mara kunya duk a inda yake mara kunya ne. Bai taba zato zata iya ci gaba da duban idanun wani daya shafi ahmad ba balle ta nuna fake love din da take masa,ciki kuwa harda akhnan din. Akhnan din daya gama fahimtar wasan data shiryayi da Rayuwarta ba qarami bane,CETONTA ko shine ya zama silar tsoma qafafunsa kenan cikin agadez?. Dab da isarsu airport din ya waiwaya a hankali zuwa sashen da take zaune. Kowacce rana tana sake tabbata ITA DIN MALLAKINSA CE......a yanzun gata sukutum da guda gaba dayanta sultane ya damqa ragamar Rayuwarta a hannunsa da dukkan yarda. Zai iya tsallakewa kuwa?,zai iya cinye wannan jarabawar?. Baya iya ganin fuskarta......amma yana iya ganin zara zaran yatsunta data gamesu guri daya tana murza zoben dake tsakiyar yatsan nata. Koda baya ganin fuskarta yana jin akwai hawaye me yawa kwance cikin fuskarta. Idan tayi kuka yanzu......idan a yanzu tana kuka kadai saboda barin agadez.......me zataji?,yaya zatayi a sanda tasan wacece mammina?. Wani radadi takeji da zugi cikin ranta....wannan tsohuwar aqidar wannan tsohon ra'ayin yanason yunquro mata. Ya rabata da mahaifarta......ya rabata da kowa nata......ya dauketa cancakat zai kaita qasarsa garinsa ba tare da tasan wayeshi ba....zai kaita inda ba idanuwan sultane babu kulawarsa......dukka don kawai buqatar kansa?,duk kawai don shi yazo a NAMIJI?. Tun daga mataki na farko.....tun a yanzun da mintuna da awannin kasancewarsu tare suka fara harbawa,ta fara lissafawa da qididdige yadda abubuwa masu tarin yawa nata suka fara juyewa zuwa MALLAKINSA ciki harda nasabarta da sunanta. Iya wannan abun tunanin dake zukatansu ya wanzar da wani irin shuru,wanda bai yanke ba sai sanda suka isa airport din bangaren private parking lot na airport din. Dukka motocin suka tsaya,sai a sannan ta daga blue eyes dinta a hankali tana duban airport din. Mamaki kadan ya kamata,kaman idan taji daidai zasu wuce Niamey ne a mota saboda ba jirgin da zai tashi a daidai wannan lokacin,amma me sukeyi cikin airport din. Bata kalleshi ba,amma tana jin sanda driver ya fice daga motar daga can bangarensa,motar ya zamana daga shi sai ita kadai. Wani shurun ya sake ratsawa tsakani,tana jin kamar wani sabonshi ne,ya kuma zame masa jiki. Jinkirin fita a duk sanda sukazo wani guri,har sai kusan wanda ke dakon fitowarsu hankalinsa yakau. A baya yana bata haushi da hakan da yakeyi,amma a yanzun saita tsinci kanta da lalubar dalili?. Izza ce ko kuwa?. Qasaita ce ta masa yawa?,wanne irin izza ne wai a jininsa?. Tambayar data fusgeta har takai ga daga idanunta da har yanzu taketa ririta hawayen cikinsu ta kalleshi. Kaman ko yaushe,kaman yadda ya saba mata,wannam attitude din nashi dake bata haushi. Ba ita yake.kalla ba......wayarsa yake kalla. Ba ita yake kalla ba,hankalinsa ba'a kanta yake ba. Me yasa sai ita zata dinga kallonsa?,me yasa sai ita zata dinga satar kallonsa?. Hasalima ai sultane tasan ya basa amanarta. Me yasa bazai damu da ita ba?. Irin duk motsinta dinnan idanunsa yana kai?,irin duk wani tari nata ko qanqani ne ya tamabaya. Wuf tayi ta zare idanunta daga kansa sanda yake motsa manyan idanunsa yana dagasu xuwa kanta. Kafeta yayi da kallo sanda take dauke idanunta cikin basarwa. Ya jita.....yaji duk wani kallonta a kansa,har iya tsahon mintunan data dauka din. Bata zata ba batayi tsammani ba taji hannuwansa saman kanta.....dukka hannuwansa guda biyu inda yasa yatsunsa yana jan bannan veil da tayi rolling dashi saman kanta. A nutse ya ajiye idanunsa gaban goshinta,inda wani sashe gashinta me santsi da baqi ke kwance luf gaban goshinta. Irin sumar nan ta cikakkiyar buzuwa da tayi gadon suma ta kowanne bangare. Bugun zuciyarta ya tsaya na wucin gadi,ta dauke numfashinta dif tana jin yadda zuciyarta ta dawo aiki da wani irin gudun wuce sa'a sanda ya sanya yatsansa a hankali kamar me tsoron taba qirjinta yana sakin tattara tattarar da mayafin yayi saman qirjinta. "Bazan iya jure wannan shigar ba......material na abayar nan yana showing........" Sai kuma ya dakata yana jan jikinsa baya. Ko da ba gaya mata ba,tana jin yadda kalmomin da haruffan suka fito a rarrabe,kamar bugun zuciyarsa keson hana sautinsa fita daidai. "Subhanallahil azeem" Yake fadi idanunsa a lumshe,yana jin yadda bugun zuciyarsa ke rarraba numfashinsa. Tsahon wasu sakanni,sannan ya bude idanunsa a hankali. Abubuwa da yawa,abubuwa da yawa ya gani saman fuskarta saboda wani irin kusanci daya wanzu tsakaninsu sanda yake qoqarin daidaita komai nata kada wani sashe na Jikinta ya bayyana. (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) Wata irin glowing skin dake shimfide saman fuskarta,wasu irin eye lashes da eye brows da suka kusa hadewa da junansu. Wata irin lobawa daga tsakiyar habarta harma da gefan kuncinta guda daya.....ga kwantaccen sumar data yiwa goshinta ado daya tabbatar ta sauka har kusa da kunnenta. A nutse ya bude murfin motar,ya fice,ta bude idanunta a sace tana kallonsa. Takunsa na dabanne......wani irin taku da tunda take ganin nau'in isassun maza bata taba katarin ganin wani da irinsa ba. Tayi gaggawar kauda kanta sanda ya iso bakin qofar da take zaune,ya saka hannu ya bude mata murfin motar kamar yadda ya saba yana ja da baya don bata hanya. Ta gefe ta sake satar kallonsa,still ba ita yake kalla ba,ya tsaya kawai daga bayan qofar da wannan wayar dai a hannunsa. Saita dauke kanta ta hadiyi wani yawu da haka kawai taji ya mata tauri da d'aci. Ranta taji ya dan jagule,ta motsa a nutse tana sako qafafunta waje,daidai nan ya matso da sauri,ya sanya hannunsa da nufin ja mata rigarta ta sauka ga qafafunta,idanunsa suka sauka saman fararen qafafunta masu dogayen yatsu wadanda jan lalle ya yiwa wani irin ado me daukan hankali.. *M A M M I N A* Bayan juyawarta zuwa cikin gidan sai takejin iskar gidan yau kawai ta dabance,kaman yadda ta tabbatar nishadinta zai zama na dabanne. Almaz yana maqale a ranta,saidai tana ganin abune me sauqi bazai zame mata matsala ba. Ta sanshi tun yana qanqaninsa,duk wata tarbiyya da raino nasa itace ta bada wannan horon,ta yaya dabbar daka raineta da hannunka ta isa ta zame maka barazana?. Ta tabbata ta kuma yi imani haisam baisan me yakeyi ba.....kodai lissafi ya kwance masa,ko kuma tsananin murnar samun akhnan......akhnan din da yake kalla kamar banza ta samu sama taka ya sanya ya soma daburcewa a lissafinsa. Wanda ita hakan yayi mata daidai,akhnan zata zama tamkar fatsar da zata kamashi a hannunta tayi wasa sa rayuwarsa har sai yayi nadamar ajiye malinta ya dauki bangaren bin diddiqinta. "Allah yaja da ran giwa.....Allah shi riqa miki" Maher.....maher d'aya daga cikin irin da haisam ya bari agadez......maher din da a yanzu mammina ke hasashen sakashi a gaba ya maye wasu gurabe na mutanen data rasa ya furta maganan cikin tsananin girmamawa. Murmushin jin dadi ta saki,yaron yana ranta tana jin kuma wani aminci a kansa,saidai duk da haka ta dakata ne ta gama karantarsa. Sau da dama yana cikin wadanda ba'a gulmarta idan an ganshi,saboda yadda yake girmama sunanta ma kadai da duk wani abu daya rabeta ballantana ita kanta. "Me yake tafe dakai?" Tafisu ta tambayi maher. "Yan jarida ne.....daga gidan talabijin da radio na qasa.....sukeson tattaunawa dake" Ta danyi jim tana duban maher din. "Tattaunawa?" Ta tambaya cikin son qarin bayani. Kai ya gyada. "Itafa Allah ya baki yawan rai......qoqarinki da jajircewarki akan mutanen qasarki da yankinki.....labarin alkhairanki daya karade ko ina shine silar zuwa su tattauna dake,sunce ki musu afuwa basu sanar ba basu nemi izni ba kafin yanzu.....amma a yanzun ma idan kina ganin saidai suje su dawo a basu lokaci zasu aikata hakan" Ya qarasa fada yana karantar yanayinta. Shuru tayi na daqiqu,shurun da tafisu ta katseshi ta hanyar fadin. "Ba girmanki bane....karamci ne a tare dake ki karbi baqin da suka zabeki ke kadai,duk da ba ke kadai bace matar sultane amma sukace dake sukeson ganawa". Murmushi ta sake saki a hankali,tafisu tazo da magana. Wannan dalilin ya sanya takeson tafisu sama da kowa cikin mutanenta. Tana da wani irin hasashe da hangen nesa me zurfi. "A basu guri mafi kyawun dauka.....zan shiga ciki na canza saina fito". "An gama Allah ya taimakeki sarkin karamci" Maher ya fadi yana miqewa sa gaggawa. A yau sai ta sakejin kanta yana fasuwa.....bawai don bata taba hira a kafar yada labarai ba.....aah,saidai wannan din tazo mata akan gabobi masu yawa,tazo mata da wata babbar dama da zata isar da wani saqo cikin sanyin rai. Sutura ta alfarma tasa aka sake ware mata,tasa kuma akayi aiken kabakin arziqi ga tarin masu daukan rahoto da labarai daga gidajen tv da radio masu yawa bisa jagorancin babban gidan jarida na qasa. Tasa a shaidawa sultane zatayi ganawa da 'yan jarida,bai kuma hanata ba tunda kusan lokaci lokaci tana yi din. *zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 08187255862 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 08187255862 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 19* Bata dauka haka yawan adadinsu yake ba sai data fito zuwa gurin,fitowartata kamar waa shugabar qasa hasken camera ya fara haskawa tako ina na masu qoqarin daukan hotonta. Har qasan ranta taji dadi.....har qasan ranta kuma taji ta sake fashewa da wani irin taqama izza da alfarma,sai data zauna sannan kowa ya zauna suka sake miqa gaisuwa bisa wakilcin mutum daya. Ta amsa musu da salon amsawarta dake dauke da izza da kuma son nuna ita din macece me kirki,kuma ita ta kowa ce,daga bisani ta basu dama,wanda kuma ya kasance shine me wakiltarsu gurin mata tamabayoyi ya matso ya soma gabatar da kansa. Tambayoyi ne daya bayan daya suia fara mata kan irin ayyukan da ita kanta take gudanarwa al'ummarta. Daya bayan daya take zaqulo dukka ayykan da tayi,manyan ayyukan da dukkaninsu tana yinsu ne saboda ta sake kafa kanta......tana kuma yinsu ne saboda biyan wata buqata ta qashin kanta. Sai da suka shafe sama da sa'a guda kowanne gidan jarida yana nadar hirar,bayan data dakata alamun da suke nuna takai aya,sai ya saki murmushi. "Dole al'ummar agadez dana nijer gaba daya su dinga alfahari da wanzuwarki a cikinsu. To amma kuma idan ba damuwa,ko zamu iya sanin asalin salsalar tushenki?" Yayi maganar da sautin daya buga amsa kuwwa cikin dakin taron. Wani irin dummmm taji cikin kanta,zuciyarta ta wani irin mahaukacin bugawa da har taji kaman tana neman amayota ta wuyanta,sai kuma tayi saurin controlling din kanta sanda ta tuna adadin cameras din dake gabanta ta saki murmushi. "Ina zaton baka dade da shigowa agadez ba.....ko kuma kai din baqo ne ko?" Idanu yadan zuba mata,sannan ya saki murmushi yana cewa. "Allah ya taimakeki.......cikkaken haifaffen nijer nake......tun daga kakana na goma zuwa yau.....kawai dai munaso muji daga bakinki ne" Kai ta jinjina tana qoqarin boye fushinta akan yaron,don a ranta sai takejin kamar baqar magana ya gaya mata. "Ni dinma kamar kai,haifaffiyar nan ce kaka da kakanni.....bansan wata qasar ba bayan wannan......basan wasu al'ummar ba bayan al'ummar qasata ta nijer.......wannan ya sanya nake tsananin kishin mutane na" Ta qarashe da murmushi. Tafi kuwa suka dauka gaba daya,abinda ya bata relief sosai taci gaba da binsu da murmushi tana addu'ar tambayar ta tsaya iya nan,saidai fatanta da addu'arta basu cilla ko ina ba wata tambayar ta sake shigowa. "Naji dadin wannan amsar taki,saboda a guraren hira daban daban,wasu na yad'a qarairayin kamar ke din baquwar haure ce iyaye ko kakanni suka shigo" Kai ta gyada cikin nutsuwa. "Tom....naji dadin haduwarku da adadi me yawa haka......yau zan tabbatarwa da duk me kokwanto qasata da asalina" Saita waiwaya tana duban tafisu,tayi magana da ita qasa qasa,tafisu ta tashi ta wuce,ita kuma ta maido hankalinta kansu. "Ku jira lokaci kadan,zan baku takardun da zaku yada don kauda wannan zargin daga zuciyar kowa" Ta qarasa fada tana murmushi,duk da zuciyarta cunkushe take da haushin yaron daya tsiro da tambayar,kuma wani irin zargin me qarfi taji ya d'arsu a ranta game dashi,gwara ta nuna musu cikakkun takardunta don kashe wannan rade radin da bataso yayi nisa ko kadan. Ci gaba tayi da amsa tambayoyinsu na daban,har zuwa sanda tafisu ta qaraso gurin. "Miqa musu su shaidawa duniya" Mammina ta fada tana murmushi. Kai tsaye kuwa tafisu harda tuntuben da mammina ta yaba dashi,ta kuma fassarashi dukka cikin saurin isar da saqonta ne ya kawo hakan ta miqawa dandanzon 'yan jarida takardun. Sannu a hankali suka bude takardun,cikin qasa da mintuna uku suka fara zagayawa a tsakaninsu,wannan ya duba ya miqawa wannan,sai wasu daga cikin su suka fara daukan hotunansu suna miqawa 'yan uwansu. Ko kusa ko alama bata kula ba,saboda sauran tambayoyin da take amsawa wani d'an jarida daban daya karbi ragamar tambayoyin,har sai da taji kamar sautin maganganu qasa qasa ya fara tashi a gurin. Idanunta ta aza a kansu,takardun sun fara nisa daga mutanen dake gaba gaba zuwa baya. "Bakusan a inda kuke bane,bada hujja zai zama kuna yawo da takardu masu muhimmanci haka a tsakaninku?" Tafisu ta fada cikin tsare gida,ta kuma fadi abinda mammina keson fada musu kenan. "Kiyi haquri.....wani abune yadan rikitar damu,banbancin bayanai ne,bayanan da uwargida ke fada yasha banban matuqa da bayanan jikin takardar" Ya fada bayan ya karbo takardun yana sake kallonsu a hannunsa. "Kamar yaya?" Mammina ta samu kanta da yin tambayar kai tsaye ba tare data jira tafisu tayi mata tambayar ba. "Kiyi haquri ki sake dubawa ranki ya dade......takardu ne na qasar Ethiopia,cikakkiyar shaida.....shekarun haihuwa takardar haihuwa ta asibiti original ba jabu ba,harda sanya hannun shugaban qasar dake tabbatar da takardun na asali ne daga tushe ma". Batasan ta miqe ba,batasan kuma ta isa gaban tarin cameras din dake zagaye da ita ba ta, saka hannu ta fusgi takardun cikin fushi. Gani take qarya kawai yake mata,gani take kawai ya fada ne saboda ya rikitar da ita,ya fada ne saboda alamunsa sun nuna akwai mummunan quduri a tattare dashi. A birkice take kallon takardar kamar wadda bata taba karatun boko ba. A gigice take bin rubutun daki daki tana karantawa. Takardar zama haifaffiya kuma mallakin qasar Ethiopia ce tabbas a hannunta,kamar dai yadda dan jaridan ya fada da farko. Idanunta ta daga tana duban tarin tulin 'yan press din da kowannensu shima ita yake kalla. Ta bisu daya bayan daya da idanu. A qalla sunkai mutum ashirin,daga mabanbantan gidajen tv dana radio. A cikinsu batasan adadij mutanen da suke da hoton takardar ba. Batasan adadin mutanen da suka watsa hotunan a take daga daukarsu ba,don ta tabbatar,babu ta yadda za'ayi labari me dumin gaske irin wannan ya shiga hannun d'an jarida ya kwana lafiya. "Ranki ya dade......nace kodai akasi aka samu?,zaki iya mana cikakken bayanin ya akayi haka ta faru?" Ya sake cusa mata tambayar yana saita camera dinsa. Idanu ta zuba masa da wani irin wulaqantaccen kallo. Ta sani.....taba d'an jarida abune me hadarin gaske,bashi kadai bama harda iyalinsa gaba daya,koda shi daya ne a guri ballantana gurin cike yake da abokan aikinsa?. "Ayimin afuwa.....wataqila takardun sun cakuda da wasu,zan nemeku idan komai ya daidaita" Abinda ta fadi kenan,bata kuma tsaya jira ba,bata tsaya jin tarin tambayoyinsu ba ta juya a gaggauce tana wucewa. Tana iya jin muryoyinsu suna jefa tarin tambayoyi mabanbanta,to amma ko tsaiwa qafafunta ba zasu iya ba ballantana ta fuskancesu. "Tabbas..... Akwai wanda yayimin kutse dakin ma'ajiyar sirrina......tamim!!!!.....zaka mutu,tabbas zaka mutu idan baka bincikomin abinda ke faruwa ba,bayan komai a hannunka yake?!" Ta fada cikin qaraji kaman wata tababbiya. Cikin kanta da ranta takejin tabbas idan har an taba wannan dakin......to bata da wani sauran qwarin gwiwa. Ta jima tana saka ranar da zata shiga ta kwashe wasu kaya a ciki ta qonesu amma sai ta manta.....don ta tabbatar wanzuwarsu a tare da ita mugun hadari ne,duk da tasan tayi kafuwar da babu me banbareta cikin agadez. Ko bayaga haka,idan an matsanta banbareta,to bomabomai ne zasu dinga fashewa daya bayan daya da sunan sarkinsu dama diyar da yafi qauna duk duniya. Hannunta har rawa yake sanda ta karbi takardar da tamim ke miqo mata sanda yake shigowa dakin da wani irin kwantaccen tsoro saman fuskarsa. Jikinsa dukka rawa yake,kaman yadda haqoransa ke haduwa kaf kaf kaf saboda tsananin tsoro kaika dauka wanka aka masa da ruwan qanqara. *_Bismillahir Rahmanir rahim_* *_Wamay yihinullahu fama lahu mimmukrim_* *_Alaisallahu bi khafin abdah?_* *_SHEIKH MUHAMMAD HAISAM MOTI ABA JIFAR IBRAHEEM the silent one_* Duk da cewa sakin layin qarshe na takardar kawai ta fahimta.......wani irin girgiza zuciyarta tayi. Sunan IBRAHEEM kadai wata babbar barazana ce ga zaman lafiyarta......ballantana ta ganshi hade da sunan da dazu dazu ta gama bankwana dashi cike da farincikin ya tafi babbar dama ta samu a gareta. *_Shin ubangiji bai isarwa bawansa ba?_* *_Dukkan wanda Allah ya wulaqanta lallai bashi da wani wanda zai girmamashi_* wannan sune fassarar abinda ke rubuce a tarin tulin takardun nan" Tafisu ta fada tana sake nutsa hannunta cikin takardun da dukkaninsu rubutu daya ne a ciki,kuma sune suka maye gurbin duk wani file da a cikinsa a baya can muhimman takardunta ne a ciki. "Innalillahi......na shiga uku!" Ta samu kanta da furtawa,a karon farko da rauninta ya bayyana muraran,ta sulale tana zama dabas a gurin a gaban tamim da tafisu tana manta meye ma matsayinta!!!. ★★ Karo na farko a rayuwarta da takejin wani namiji haka dan da dab kusa da ita. Karon farko kenan da takejin wani irin kariya da tsaro suna bibiye da ita. Dukkan wani taku nata qwaya daya da zata sauke zaya sauke nashi a tare da ita,hakanan koda wani sashe na mayafi ko abayarta ya tattare tana iya jin yadda hannunsa ke kaiwa gurin ya gyara zamansa sosai a jikinta. A duk sanda yayi hakan......wani abu daban yake saukarw a jikinta da ruhinta.....wani yanayi takeji na izzar da bata tana jin makamanciyarta ba. Tun daga faarfajiyar airport na agadez bata sake saka falaaq da maleek a idanunta ba,bawai don ta damu ko akwai sabo da shaquwa me yawa ba.....aah,haka kawai lokaci lokaci sai zuciyarta ta gaya mata a yanzun bata da wani sama da falaaq din. Blue eyes dinta ta daga a nutse ganin ba wani cikowa ko mutane.......karo na biyu wani mamakin ya kasheta bayan wanda ta shiga a airport na agadez ganin private jet din da daga ita saishi ya daukosu ya kuma ajiyesu a nan Niamey din. "Private terminal?" Ta fadi a hankali idanunta akan private jet na biyu da suke tunkara wanda yasha banban da wanda ya kawo su Niamey din. "Me yake faruwa?" Ta furta can qasan ranta. "Alfarma ce dashi haka?" Ta sake tambayar kanta da kanta daidai sanda sauran ma'aikatan dake gurin suke gaidashi cikin tarba ta musamman da kuma girmamawa,saidai duk maganan da suke kaman a agadez da wani yare ne da bata jinsa bata kuma ganewa,amma yanayin girman da suke bashi sai abun yake sake jefata cikin duhu. _yanzu kika fara shiga duhu akhnan?,ko baki fara shiga bama?_ *_yan uwana masoyana assalamu alaikum warahmatullah_* *_gaisuwa da fatan alkhairi,biki gareni na sisters dina har biyu,ina neman uzuri da afuwa idan har kuka jini shuru laraba alhamis da juma'a,duk da zanyi dukkan qoqari tuquru naga ban tsallake muku kwanakin ba in sha Allah,saboda halin rayuwa da yanayin biki,amma koda page bibbiyu ko daya daya ne ya samu zan qoqarta kada na barku haka_ _na gode muku qwarai da gaske,in sha Allah huguma ba zata baku kunya ba_🙏🏽🙏🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 20* *_Assalamu alaikum warahmatullah_* *_welcome back diaries,na gode sosai da tarin addu'o'inku ga amare,mun kammala lafiya alhmdlh,Allah ya qara zumunci ya sassaka muku da alkhairi_* Har cikin qasusuwanta wani irin mamaki yake ratsawa,mamakin da ya sanya takejin wani irin yanayi na rashin sakewa a tare da ita. "Bonsoir, Madame. Soyez la bienvenue. Permettez-moi de prendre votre bagage(barka da yamma madame,muna miki barka da zuwa,ki bani dama na karbi jakarki)". Taji an fada cikin girmamawa. A hankali ta daga kanta zuwa fuskar wadda ke maganan. Daya daga cikin ma'aikatan jirgin ce,matashiya fara sol da ita,wadda koda ba'a gaya maka ba zakasan cewa bata hada komai da qasara niger ba. Saidai tana da wani irin kyau da kuma zubi na BUZAYE. Yana shigarta riga da skirt ne da kana kallonsu kasan uniform ne,saidai sun fidda shape dinta,sun mata kuma wani irin mugun kyau. Qaramin hijab ne a jikinta da bai kammala rufe qugunta ba,sannan bai hana idanu su gane irin shape da kyan da take dashi. Idanunta akhnan ta dauke a hankali,da salon izzar nan tata daya zame mata al'ada kuma dabi'a ta miqa mata jakar ba tare da tace mata komai ba. Kadan ta rusuna,sannan ta saka hannu biyu ta karbi jakar,saidai kafin ta juya gaba daya saita waiwaya sashen da haisam yake. "BonBonsoir, Monsieur.” Ta furta a ladabce tana rusunawa tana duban haisam din. A nutse akhnan ta daga idanunta tana satar kallonsa ta gefan idanunta da wani yanayi,yanayin da batasan me yaja hankalinta zuwa gareshi ba sanda crew din ke gaidashi ba......batasan me takeson gani ba,amma tanaso taga fuskarsa ne haka kurum,tana so taga idanunsa. Murmushi kadan yayi,cikin nutsuwa da kamewarsa dinnan. Har kayi zaton kamar bazai amsa ba sai kuma muryarsa me cike da tarin nutsuwar nan ta motsa. "Bonsoir" Wani irin numfashi taja,numfashi me nauyi,a karon farko tana juya "Da gaske numfashi yana nauyi a qirjin mutum" Wani abu yana matse zuciyarta . Murmushinsa......wani abu da ba zata iya tunawa ta taba gani ba a tattare dashi. Zata iya cewa ma bata taba ganin ba kai tsaye,tafi ganin izzarsa......tafi ganin qasaitarsa.....tafi kuma ganin girman kansa a fili sama da komai. "Ya kalleta bayan ta kalleshi" Wata zuciyar ta gaya mata a hankali. Saita tuna,sau nawa tana satar kallonsa ita amma sai taga ba ita yake kalla ba?,sau nawa tana saka ran ganin idanunshi a kanta amma sai ta tarar ba ita yake kalla ba. Me yasa?,me yasa ya daga idanun nan nasa masu girma ya sauke akan crew din.....me yasa itama take kallonsa haka?. "Me yasa kika damu?" Tambayar da zuciyarta tayi mata kenan,tambayar kuma data sanyata saurin dauke hankalinta daga gurin kamar ba komai,saidai har yanzu matsewar nan da qirjinta yayi bataji ya saki ba,musamman data hangi murmushi shimfide saman fuskar crew din data fara takawa a hankali. "Zan iya riqe jakata" Ta furta da hausa a wannan karon tanason lissafi wanne yare ce matar?. Tsayawa tayi cak crew din,yaji saukar maganar a kunnensa......amma yayi kamar baiji ba "Bien sûr madame" Ta fadi da girmamawa tana miqa mata jakar da hannu biyu cikin girmamawa. Fuskarta a dinke tsaf take takawa tana biye dashi,saidai kuma a hankali ta fahimci ya sassauta yanayin qasaitacciyar tafiyar nan tasa,a hankali ta riskeshi......a hankali kuma ta daidaita dashi,sai a sannan kuma ta fahimci jerawa yake nufin suyi. Idanunta zube a gabansu,tana hangen wasu mutane dab da private jet din tsaye cikin sahu da wani yanayi na girmamawa. Idan ta lura da kyau,dukkaninsu sanye suke da kalan kala guda daya. Baqaqen suit da farar shirt daga ciki. A hankali takejin iska tana shigar da qamshin nan nasa sosai cikin hancinta,qamshin daya tabbatar mata ya sake matsowa dab da ita ne,kafin kuma tayi kowanne motsi ta tsinci lallausan tafin hannunsa cikin nata. Wani abu ya tsarga mata tun daga kanta zuwa tafin qafafunta,wani abu me kama da magnet daya tilastata lumshe blue eyes dinta tana kuma sauraron wani irin bugu da zuciyarta keyi. A hankali taji ya zame jakar hannunta data karba daga hannun crew din,ya maidata daya hannun nasa,sannan ya sake dawowa da hannun nasa yana sake cusashi cikin tsakiyar tafin hannunta. Wani abu ya ratsa tsakaninsu,tun daga tafukan hannuwansu zuwa sassan jikinsu,wani irin dumi wani irin yanayi daya sake sanyawa tafiyar tasu ta sake zama very slow. Yana ji a ransa kamar ya murza tafin hannunsa sosai cikin nata,yana ji kamar ya manna tafin hannun sama da yadda ya manna a yanzu. Wani abu yakeji da bai taba jin irinsa ba......wani irin yanayi.....wani irin dumi tsakiyar tafin hannun nata da yake da dan damshi na gumi kadan. Yanayi ne da bai taba jinsa a tafin hannun kowa bama. To ta yaya ma zaiji?,bayan shi din koda huldar data shafi mata baya ciki ballantana yakai ga riqe hannun diyar kowa?. Idan da tafin hannun daya sani na 'yan uwansa ne maza yayin musabaha. Sukam ba wani wan yayi koda shige da irin wannan tafin hannun ballantana kamanni. Cak ya dakata da tafiyar,abinda ya tilastata tsaiwa kenan,yayi taku biyu ya matsa gabanta kadan,dukka hannuwansa ya sanya ya jawo veil din kanta sosai yana rufe fuskarta kafadarta da qirjinta. Idonta ta lumshe......tana jin wannan kusancin dake tsakaninsu......tana jin wannan qamshin wanda a yanzu yake cakude da dumin numfashinsa yana sauka daga saman goshinta ya gangaro zuwa hancinta saboda tsaho daya d'arata dashi. Sau tari tana raina tsahonta a duk sanda take tsaye haka a gabansa. Bata gane tsahonsa saita tsaya a gabansa taga yadda ya kere mata. Ta lura dashi.....giant ne.....wani irin giant dake da wahalar samu.....wani irin giant da tsahonsa ya dace da murjewar jikinsa,harma ba zakaga tsahon ba sai sanda kayi gigin hada kafada dashi. Wani rawa taji qwayar idanunta sunayi sanda taji hannuwansa saman kafadarta,idanunta kan tsakiyar qirjinsa wadda data matsanta zubawa idanu taga yadda qirjin nasa yake motsawa da yanayin bugun lafiyayyar zuciyarsa. "Boundaries please" Ya fada a hankali idanunsa suna lumshewa a cikin nata. Baisan wanne irin kishi Allah yayi masa ba,baisan wacce irin zuciya ce dashi haka ba......baisan me yasa ba,ko yaya yaga zashi doshi wani guri da ita,wani guri da yake cakude da maza sai yaji zuciyarsa tana matsewa. Yadda yayi mata magana idanunsa cikin nata......yadda ya furta haruffan da wani irin sanyi da taushi......ta fahimceshi,ta fahimci me yake fada,duk da ba turanci ne yarenta ba,amma tana gane da yawa daga cikin maganan da za'ayi mata dashi sama da yadda zata maida. Kasheta kawai takeji yanayi da idanunsa.......wani irin abu takeji yana saukar mata,abin daya soma narkar da wannan zafin da taji ya tsaya mata a wuya sanda crew din ke magana dashi. Still bai zare idanunsa daga nata ba.....ya sake miqa tattausan hannunsan nan da baya rabo ko yaushe da qamshin wani tsadajjen misk,dalilin da yasa komai ya riqe,kuma komai zai riqe koda na second daya ne qamshinsa daban yake. "Muje" Ya sake fadi da wata murya da a yau takejin ta mata ta daban. "Welcome sir" Kalman farko data fara ji dukkaninsu suna fadi kenan da girmamawa suna rusunawa. "Sir?" Ta sake fadi can qasan ranta tana kuma maimaita kalmar,kamar dai yau ne karon farko da tasan kalmar a rayuwarta. Tun daga isowarsu bakin jirgin......takawarsu zuwa ciki da shigarsu sai komai ya sake tsinke mata. Wani irin luxury sofas jet din yake dashi......wani irin tsari da sam bai mata kama da tsarin jirgi ba,sai qananun gidaje na alfarma da aka tsara saboda hutawar gangar jiki da ruhi. Cikin wani yanayi dake nuna zallar girmamawa,girmamawar data tilastawa akhnan satar kallon duk wani motsinsa pilot dama crew din da zasu kasance dasu cikin jirgin saboda hidima garesu suka gabatar masa da kansu gami da sake gaidashi. "Na gode......ina fatan zakuji dadin tafiya dani" Ya fada da wani lallausan yanayi dake nuna zallar sanin kima da darajar dan adam. Murmushi wasu sukayi da 'yar dariya,sannan daya daga cikin pilot din ya amsa masa. "Karramawa ce a garemu yin tafiya tare dakai ranka ya dade" Ya fada yana rusunawa,sannan a hankali suka fara jayewa suna basu guri. "Ranka ya dade" Ta sake nanatawa a hankali cikin kanta. Ta sake lumshe idanunta tana jin yadda wannan lallausan qamshin nasa......wannan turaren nasa yake sake cika jirgin,yake kuma sake cika inda suke zaunen,wanda banda window din da take iya hangen farfajiyar airport din ba zaka taba yarda cikin jirgi kake ba,don yafi mata kama da wani qawataccen parlor na alfarma. Ta runtse idanunta a hankali sanda jirgin ya soma motsawa. A hankali zuciyarta ta danyi wani nauyi tana jin yanayin bugunta yana sauyawa. A yau itace zata bar agadez?......sannan kuma tabar Niamey gaba daya?. Yau zata bar sultane?.....zatabar company dinta......zatabar masarauta.....zatabar mahaifarta inda cibiyarta take. Zata bar kowa......zata bar komai,ba tare kuma da cikakken bayanin yaushe?......a wanne lokaci zata sake dawowa cikinta ba?. Suwa zata samu a can inda zataje?,wacce rayuwa zatayi dasu?,dukka bata da wannan amsar kwata kwata. A nutse ya kammala saka seatbelt dinsa,ya daidaita zamansa sanda jirgin yake ci gaba da saita gudu saman kwalta na adadin mintunan daya saba gabanin cirawarsa zuwa sama. Ya juya a nutse yana sauke idanunsa a kanta. Idanunta a lumshe suke,ta rufesu ruf,kaman yadda ta karkatar da fuskarta kadan zuwa window,saidai hakan bai hanashi ganin fuskar dama abinda ke shimfide akai ba. Wani abu yaji ya sauka saman zuciyarsa a hankali,wani abu daya tuna masa da kalaman sultane. Amana......ya damqa amanarta a hannunsa.....eh koda sultane bai fada ba ya sani,mata amanace a hannun mazajensu,duk wanda ya cutatar ko ya quntata akwai mummunar makoma da sakamako akansa. Basu da qarfin komai.....basu da qarfin ikon yin jayayya ko challenge naka......amma suna da me qarfin masu qarfi daya tsaya musu. A nutse ya miqa dogon hannunsa yana zagaye qugunta dashi don ya ciro seatbelt din da baiga tayi koda alamun sakawa ba. Yanayin daya haifar da wani irin kusanci me girma a tsakaninsu,yanayin kuma daya qara gudun zuciyarta dake lullube a qirjinta saboda hucin duminsa da taji dake gauraye da turaren nasa. Ta bude idanunta ne da sauri don tantance me yake faruwa. Kai tsaye idanun nata suka sauka cikin nasa.......wadannan idanun da suka zama idanu na farko da suka fara yi mata nauyi cikin kanta. Idanu na farko da suka fara sakata abu ko su hanata ba tare da mamallakin idanun yace komai da ita ba. Idanun da sukayi wata ajiya me girma cikin kwanyarta dama zuciyarta. Har yanzu still,ba wani abu daya canza.....har yanzu suna da wannan nauyin da ba zata iya jurewa kallonsu ba......dole ta maida nata idanun ta sake lumshesu a hankali kamar wadda kejin bacci,yanayin daya bashi daman dora qwayar idanunsa saman qirjinta,kallonsa ya sauka a kansu da wani irin sassanyan yanayin daya harba wani abu me tsananin qarfi zuwa ga sassan jikinsa. Wani irin girrr hannayensa sukayi kaman wanda wutar lantarki taja sanda ya zagaya daya hannun nasa zuwa gefan qugunta yana soke belt din,abinda ya sanya jikinsa ya shafi tudun qirjinta kenan,tudun daya narkar da wani abu guda dake tsaye kyam a zuciyarsa wato JARUMTA. Bashi kadai ba......ita kanta taji.....taji reaction na jikinsa,saidai tsoron daya saukar mata itama ya sanya bata fahimci komai ba,sai daukewar da numfashinta yayi na daqiqu. Komawa yayi ya zauna sosai saman seat dinsa yana qoqarin saita nutsuwarsa. Idanunsa sukayi laushi sosai lissafin abubuwa yana cika kansa. Ya sani.....akwai manufar aurenta. TARKO.....tarko ne ga mammina da zuwa yanzu ya kammala da babinta......zuwan wa'adin fashewar nakiyoyin daya dasa kadai yake jira. Nakiyoyin da ya sani......da kanta zata sanya abu me qarfi ta dinga fashesu daya bayan daya.....a yanzun a qulle take cikin wani irin dabaibayi sasari dama sarqoqin da ita kanta bata sani ba.......to amma wannan auren fa?.💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 21* "YA DAURU.....NA DINDINDIN NE!" Daga can wani sashe na zuciyarsa ya bashi amsa. Bai sani ba,amma ya jima yana hasashe. Tabbas akwai qaddarorin da muke saqasu da farko,amma qarshensu saisu qwace daga sarrafawarmu su shiga saqa kansu da kansu.......ko wannan shiryayyar qaddarar zata qwace daga hannunsa ne?......ta fara saqa kanta da kanta?. Tunaninsa ya yanke sanda ya soma jin wani abu......wani abu kaman sheshsheqar kuka can qasa,sheshsheqar da ake boyeta ba tare da buqatar kowa ya jita ba. Saidai shi din na dabanne,yana da wani irin kakkaifan ji,wanda zaiyi wahala kayi magana komai qanqantarta ba tare da yajika ba. Sanda idanunta ke kallon yadda jirginsu yakeyin nisa da niger.......yakeyin nisa da qasar Niamey gaba daya,sai takejin kamar tanayin wani nisa ne na har abada. Kamar tana barin niger ne bari na har abada,kamar akwai nisa da sultane zaiyi mata nisa na har abada. Kamar zata barshi ne na har abada.....shima zai barta bari na har abada din. Sai taji gaba daya zuciyarta ta karye,sai taji kaman tana da buqatar wani a kusa da ita,wanin da zatayi kuka sosai a sake a gabansa kamar sultane. Ba gaban kowa take kuka ba......ba kowa yake ganin hawayenta ba idan ka debe mutum biyun,sultane da mammina,saidai a yanzun sultane kadai take dashi wanda zatayi kuka a gabansa ta more,a ina zata samu madadi?,ta qarashe da tambayarta mara amsa. A hankali taji lallausan tafin hannun nan nasa yana kutsawa zuwa cikin nata......a hankali da wani irin yanayi ta tafiyar maciji taji yana kutsa yatsunsa biyar tsakiyar nasa yanzun.......a hankali kuma taji ya game hannuwansu guri daya yadan matse cikin nasa ta yadda suka fara musayar dumin hannuwan juna. Wani irin shuru.....shuru me cakude da nutsuwa shine abinda ya wanxu a tsakaninsu,shine abinda ya mamaye jirgin iyakar inda suke. Duk da kukan bai tsaya ba,amma wani irin sassauci takeji yana sauka a hankali cikin zuciyarta. Wani irin sanyi da ya sanya hatta da hawayen dake fita daga cikin idanunta suke fita da wani irin sanyi. Lokaci lokaci tana jin yadda yake dan matsa hannunta dake cikin nasa,kamar dai yanason yayi magana ne,kaman dai lallashinta yakeyi ta hanyar motsa yatsunsu dake guri daya da dan matsasu kadan. Tsahon wasu mintuna,kafin a hankali wannan muryar tasa me laushi da zurfi ta motsa a hankali zuwa cikin kunnenta,cikin yarenta,cikin harshen faransanci da wannnan accent din nasa dake bugar da ita,yake sake saka mata jin tsananin dadin yaren French wanda a baya batasan yana dashi ba sai a bakinsa "Kiyi kuka idan kinaso,ba rauni bane......amma bame cutarwa ba" Sai taji kalaman sun sauka a kunnuwanta da wani irin banbanci me yawan gaske. Maimakon kuma kukan yaci gaba,a hankali sai taji hawayen suna raguwa suna ja baya da kansu. Yaji komai,duk da baya ganin fuskarta amma yaji yadda ta soma daidaita kanta,yana jin nauyin wannan amanar dake saman kansa......yana kuma fatan ya sauketa har zuwa sanda Allah zaiyi ikonsa cikin lamarinsu gaba daya shi da ita. “Wani lokaci… dole ne mutum ya bar wuri… domin ya gano inda ya kamata ya kasance.” yayi maganar da nazari masu yawa cikin magananunsa,wanda ya sani,a wannan lokaci ba lallai bane ta fahimci ma'anonin maganarsa ba. Sosai maganan ya tsaya mata a rai,amma kuma ta gaza sarrafa maganar cikin ranta. Tana jin sanda ya zame tattausan tafin hannunsa daga cikin nata,sai taji yatsunta suna motsi a hankali.....suna motsawa kaman suna shirin riqe nasa yatsun da suke dab da ficewa daga cikin nata. "Ungo" Ya fada a hankali yana ajiye mata tissue. A hankali ta juyo da fuskar ta don ganin me yake miqa matan,kai tsaye idanunta suka zarce kan fuskarsa suka fada cikin idanunsa. Ita yake kalla da wadannan idanun da har abada suke tuna mata wadancan ranakun na farko. Wani lokaci idan ta motsa labbanta,sai taji tanason tambayarsa. "Kaine wannan mutumin?,na wancan ranar daya fara sanyawa na zama mara nasara karo na farko a rayuwata?." Saidai kuma kwarjininsa da izzarta suna cakuduwa su tayar da alfaharinta na diya mace,kaman yanzu saita zare idanunta daga kansa sanda ta fahimci shima ya dauke kansa daga gareta. "Assalamu alaikum sir....akwai abinda kake buqata?" Ta sake jin muryar wannan matashiyar crew din. Wani abu ta shaqa sosai cikin hancinta,ya kuma tsaye mata a qirjinta cak kaman tsaiwar mashi. "Me kuma take nema?" Taji tambayar ta zarta cikin kanta. Kadan ta matse yatsunta tanason kauda hankalinta akan komai ma,don batasan abinda yake jan hankalinta ba ga duk motsi da maganan da yarinyar zatayi masa ba. Ba tare daya amsa mata ba,ya juya kansa a hankali zuwa sashen da take. "Kina buqatar wani abu?" Ya tambayeta da wani irin softness da yaren French din nan nasa da kullum xai magana dashi sai taji kamar nasa yaran daban yake da wanda ta saba ji. Kai kawai ta girgiza masa,cikin izzarnan tata da sanyin jiki,sannan a hankali ta motsa labbanta tana cewa "Ba komai" Kaman bazai janye idanunsa daga kanta ba,kafin ya janye din,ba tare kuma daya sake duban crew din ba ya furta. "Ruwa.......coffee,in akwai buqata sama da haka zaa sanar miki" Ya fada da salon iya taqaice magana irin nashi. Kai ta gyada,sannan a ladabce ta juya tana barin gurin don cika umarninsa. Komai daya shafi jirgin.....komai daya shafi tafiyar tasu tana nuna zallar alfarma ne da wata irin tarin izza da dukiya. Wani irin yanayi da tunda take hawa jirgi bata taba riskar yanayi irinsa ba. Shuru ya wadaci gurin.........sanda jirgin ke sake kutsawa cikin sararin subhana. Pilot da crew din da basu da yawa dukka suna bangarorinsu suna ayyukansu. (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) Ta gaza controlling zuciyarta,ta gaza tsaida zuciyarta daga nanata tambayar SHI WAYE?......WAYESHI A AGADEZ......KO NIAMEY da yake da irin wannan alfarmar?. Private jet.....private pilot.......private crew?. Komai private ne.....komai kuma me kima tsada da alfarma ne. Tun bayan da ta kawo ruwan,ya tura mata gabanta......ya hada da tissue dukka ya ajiye mata,duk da cewar bata buqaci komai ba. Sai ya gyara kujerar da yake kai zuwa yanayin da zaifi masa dadin relaxing bayansa sosai. Yayi relaxing din cikin wata nutsuwa yana miqe dogayen qafafunsa dake sanye cikin socks charcoal color da suka dace da shigar jikinsa. A nutse ya bude briefcase din dake gefansa,ya zaro wani qaramin littafi da duka duka a qiyasinta shafukansa ba zasu haura hamsin ba. Daga kwancen ya sake ragewa gurin da yafi kama da parlor haske,ya koma yayi relaxing sosai yana bude littafin. Shuru ya ziyarci gurin,wani irin shuru da bai bar mata komai ba sai qamshin turarensa da kuma satar kallonsa da bata shirya ba. Tun bai jima ba ta fahimci karatun yana mata dadi,tun basuyi nisa ba ta gane yadda karatu ke matuqar dauke masa hankali da sakashi a nishadi. Sannu a hankali saita samu kanta da satar kallonsa,satar kallon data zarce mata zuwa wani kalar satar kallo na minti daya zuwa rabin minti sannan ta zare idanunta da sauri a duk sanda taga yayi motsi. Yadda fararen manyan qwayar idanunsa suka rusuna kamar wanda bacci ke son qwacewa.......ta saukar da idanunta a hankali zuwa ga lips dinsa. Wani abu daya fusgi hankalinta.....wani abu data sani ya taba burgeta sau daya tak game da wani jarumi cikin fina finan soyayyan da takan kalla. Wasu irin lips ne masu wani irin shape me daukan hankali,lips din da zai wahala kaga sun bushe,suna da wani irin yanayi dake nuna sulbin da suke dashi koda daga nesa kake,nisan da zaka dauka ma mamallakinsu yana using lips gloss ne saboda qawatashi. Ta saukar da duban nata cikin dabara zuwa ga habarsa. Wani irin beard,kwantaccen saje da gemu daya zama cikakken ado wa fuskarsa. Wasu irin gashi marasa tauri sune kwance sama da qasan labban nasa,suka kuma zagayesu sannan suka hade da kuncinsa zuwa qasan habarsa. Wani irin baqin gashi me daukan idanu da kuma sulbi a idanu ma.....sulbin da haka kawai taji zuciyarta lokaci daya na fusgarta dason taji yanayinsu cikin hannunta. Ta sake maida idanunsa ga cikakkiyar girar dake barazanar hadewa da juna,sai taji wani abu ya zarce ta cikin maqogoranta,ya kuma harba saqon. "Anya bai fini kyau ba?" Tambayar da ita kanta tasan ta sakata a shakka......shakkar da tabbaci yakeso ya rinjayeta. Ba bala'e'en kyau ya mallaka ba......amma Allah ya yiwa zubin halitta da tsarinsa baiwa da KWARJINI. Komai nasa idan ka kalla yana da wata irin cika da kamala da kwarjini. Sanda ta dora idanunta kan hannunsa dake riqe da littafin sai taji bugun numfashinta ya sauya na wucin gadi,ta janye idanunta saboda zuciyarta dake gaya mata. "Kallon bai yawa ba?.....idan yaji a jikinsa fa?" Amma haka kawai minti daya kacal sai taji tanaso ta kalla,tanason ta kalli dogayen yatsun nan da ayau suka ratsa tafukan hannayenta sama da kullum. Tanason taga yatsun da sune na farko da suka fara gauraya da nata yatsun da sunan d'a namiji ya taba hannuwan nata. Saidai a wannan karon tana shirin janye idanun nata ya kamata da nasa idanun da wani irin sauri da bazata da bata taba kawowa ba. Wani irin kunya...kunya me nauyi da wani irin sanyi taji yana bin kowacce gaba ta jikinta. Zagayayyun fararen idanun da bata taba ganin wani d'a namiji da fararen idanuwa irin haka ba. Kafeta yayi da wadannan mayatattun idanuwan nasa,idanuwan da suke da wani irin tasiri,ba iya kan mata kawai ba hatta da maza. Yana da wani irin shape ne idanunsa da wani irin tasiri da yawanci ma'abota yawan kallon alqur'ani da hadith kawai ke samunsa saboda kwarjini da albarkar da litattafan ke dasu. *zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 08187255862 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 08187255862 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 22* "Kici gaba" Ya furta a nutse yana motsa wadannan kyawawan labban nasa bayan data dauke dubanta kwata kwata daga sashen. Ita sam ba zata bari ba......ba zata aminta ya fahimci koda sau daya ta saci kallonsa ba. Maganar saita tsananta bugawar da zuciyarta takeyi bayan wadda ta tsinci kanta a ciki a dazu,sanda yayi mata kamun ba zata. Tsuke fuska tayi kadan,sosai takejin ba zata aminta kai tsaye ba. "Me?" Ta furta cikin qarfin hali da dakiya bayan ta waiwayo tana dubansa,saidai duban bai kasance nakai tsaye ba,don ta sani.....a yanayin ba zata iya kallon qwayar idanunsa ba. "Kallon" Shima ya bata amsa a yanayi nakai tsaye yana kuma sake kafeta da idanun nan nasa. Yadda ta soma amsa masan da wannan izzar.....da wannan k'i fadin.....da wannan jin isar sai yaja ra'ayinsa. Yadda zuciyarta ta sake bugawa tare da bata tabbacin ya ganta.....tabbas ya gagganta tana kallonsa. Tun yaushe?,tun kallon farko?,ko ana qarshe ne?. Rasa me zatace tayi.....rasa amsar bashi tayi,saboda ita din kanta tana mamakin ita khadeeja muhammad hammud?,......itace da satar kallon wani d'a namiji?,why?.....me yasa?. Cikin son kariyar mutuncinta da jin izza ta dauke kallonta daga sashen data ajiye kanta ta maida ga window ba tare da tace komai ba,tana kallon yadda suke keta gajimare da girgije suna sake nisa cikin sararin samaniya. Haka kawai yaji bayason maganan ya tsaya iya haka,ya motsa kadan ya gyara zamansa yana aza qafarsa daya saman daya,wani yanayin zama dake masa kyau,yana kuma sake fidda wata shimfidaddiyar izza dake tattare dashi wanda shi kansa baisan yana da ita ba. "Me kike kalla?" Ya sake tambayarta yanayin haka kawai yana sanyashi nishadi,saidai ko ga saman fuskarsa ba zaka fahimci hakan ba. Sake tsananta bugu zuciyarta tayi,ta sake tsuke fuska tana girgiza kai. "Ba komai" Ta fada cikin yanayi na basarwa,can qasan ranta cike da tuhuma. Boyayyen murmushi ya saki. Ba itace mace ta farko da irin haka ta faru tsakaninsu ba,saidai nata yanayin cike yake da wani irin izza jin kai da kiyaye pride irin na diya mace. Yanason wannan dabi'ar.......kare alfahari da izza ba,karon farko daya fara ganinta tattare da wata diya mace a kansa. "Kici gaba......amma kuma....." Sai yadan dakata. Dukka kunnuwanta suna gurin,dukka kunnuwanta suna tare da fitar lafazin daga bakinsa. Tsaiwar tasa sai tasa mata wani irin qaguauta taji abinda zaya qarasa fada,amma kuma sai ya yanke maganan daga nan. "Idan kika kalleni na dan lokaci......" Ya sake dakatawa kaman bayason ya qarasa maganan. "Bazan qyaleki ki daina ba" Da sauri ta juyo.....wani irin saurin da bata shirya ba. Hakan yakeso dama.......sosai ya riqe qwayar idanunta cikin nasa,akwai abinda yakeso ya gani,kuma ya samu ya gani din,kafin a hankali ya zame idanun nasa. Numfashi take saukewa a hankali bayan ta maida idanunta ga window,tana jin wata gajiya da tsoro suna shigarta a hankali. Qirjinta yana dagawa,haka numfashinta yana fita da wani irin yanayi kamar wadda tayi gudu. "Waye shi?,wanna irin mutum ne shi?" Tambayoyi biyun da takejin qaguwar samu amsa sosai a kansu,saidai ta sani a nan kusa bata da wannan amsar......bata dame sanar da ita. Ya kama ta tana kallonsa… amma maimakon ya dakatar da ita,ya sanya ta son sake kallonsa ne kawai......amma tana tsoron maganansa na qarshe BAZAN QYALEKI KI DAINA BA..... Cikin qasa da awa daya wani mutum daban take gani ba sheikh haisam ba......ba sheikh muhammad haisam da yake zaune a masarautarsu qarqashin alfarmar mahaifinta ba. Sanda ta farka daga baccin daya dauketa bayan shurun daya ratsa tsakaninsu,shurun da yafi mata sauqin wanzuwa tsakaninsu akan ya sake kamata tana kallonsa......ta farka ta samu kanta lullube da wani tattausan baro,kanta kuma jingine da madaidaicin pillow me taushi,kaman yadda aka sauya fasalin kujerar nata zuwa yanayin da zaiyi supporting kwanciyartata. Koda ta bude idanun nata a gabanta ta ganshi,ta waiwaya tana duban window din wanda ya gaya mata a tsaye jirgin yake. Koda ta duba lokaci sai taga sun qara kusan mintuna goma sha biyar akan ainihin lokacin da akace zasu sauka. Ya sauka jirgin tuntuni,ta sani,inde ba babbar lalura ko wata damuwa ba,jirgi baya sab'a lokacin tashinsa ko saukarsa........zaman da sukayi kenan kawai ana jira ta tashi a barcinta ne ko kuma yaya?. Ta sauke idanunta a hankali a gabanta sanda ya tsugunna da nutsuwa yana daidaita mata takalmanta a gabanta. Wani irin nauyi taji.....nauyi taji sosai ya aza mata. Anya batayi kuskuren fahimtarsa ba?, ba kowanne d'a namiji bane zai yarda yayi lowering kansa.......ya tsugunna a gabanki ya daidaita takalmanki zuwa saitin qafarki don kawai kisa ba. To me tayi masa data cancanci wannan girmamawar?. "Koyi yake.....koyi yake da fiyayyen halitta" Wani sashe na zuciyarta ya bata amsa sanda yake tuna mata da wani sashe na littafin nan data karanta. Yadda yake hidimawa iyalinsa......yadda yake iya durqusawa matarsa ta takashi ta hau abun hawa S A W. Idanunta ta lumshe tana jan siririn numfashi tana saukewa. A karon farko ta bishi da kallo,kallon dake narke da wani kalan emotion daga zuciyarta.......kallo me nauyi dake dauke da sinadaran BURGEWA......karon farko daya juya yana takawa tabi faffadan bayansa da kallo tana jin har qasan zuciyarta wata qwayar halitta me suna BURGEWA tana sauka tsakiyar naman zuciyarta. Welcome to jidda......ta gani a rubuce b'aro b'aro,sanda suke takawa ita dashi kafada da kafada kamar wanda aka bashi gadinta. Ta sauke numfashi me sanyi a karo na babu adadi. Ta dauka a Riyadh zasu sauka......su sake bin mota su shigo makka,saiga wasu irin shimfida shimfidan motoci qirar Rolls Royce Cullinan guda biyu,da tarin Mercedes Benz S-class da suka kusa guda biyar. Jerin motocin alfarma guda shida da suke tsaye cikin tsari.......baya ga mutanen da take hange. Sanye da baqaqen suits kamar yadda aka taresu a airport na Niamey.....sai larabawan da take hanga sanye da farin thobe daya dace da shigar jikinsu sosai tare da bayyana asalin gadon shigar da sukayi. Koda ba'a gaya mata ba ta gani.......tsaiwar jiransa sukeyi. Duk wanda ke tsaye a gurin dama motocin dake gurin suna jiran isowarsa ne. Kaman dazun.....kamar a Niamey,yayi taku biyu yasha gabanta,ya kuma rufeta da faffadan qirjinsa ta yadda bame iya ganinta,ya sanya hannuwansa ya gyara yafen mayafinta,ya kuma gyara mata abayar jikinta sosai. Da wani irin sanyi a muryarsa......yana jin kamar yana hadiye wani abu da qyar ya furta. "Boundaries please" Kaman dai dazun,amma a yanzun tana jin wani abu deep cikin muryar tasa. Bata sani ba.....batasan dalilin duka wannan ba. (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) A hankali ya sake ratsa yatsunsa da nata......a hankali ya sake game tafukan hannunsu da wannan yanayin da yake sakawa tsigar jikinta tayi wani irin zubawa har taji kaman karsashinta yana raguwa. Takunsu kusan daidai yake tafiya,suna sake kusantar mutanen da dukkaninsu ke murmushiwa haisam din. "Assalamu alaikum warahmatullah......welcome your royal highness" Balarabe na farko ya fara fada fuskarsa dauke da wani irin murmushi da zai nuna zallar sabo dake tsakaninsa da haisam din. Wannan miskilin murmushin......wannan miskilin yanayin dashi ya amsa masa yana bashi hannu shima. "Royal highness?" Ta maimaita Kalmar cikin kanta tana satar kallon fuskar haisam,wanda yadan taka gaba kadan da ita yana gaisawa da sauran mutanen dake tsaye,fuskar da bata samu cikakkiyar damar kallonta ba sai kwantaccen gashin gefan fuskarsa dake glowing a hasken fitilun da suka cika king abdul'aziz international airport din tamkar allurarka ta fadi ka dauka. A hankali takejin wannan nutsatsiyar muryar tasa da tasha banban data dukka mazan dake gurin tana ratsa kunnuwanta. Idanunta suna kafe a qasa,tana jin gaisuwarsu tana kuma amsawa a hankali saidai bata daga kai ta kalli koda mutum daya a cikinsu ba,muryarsa da yadda yake magana da yaren da ta rasa gane wanne yare ne kawai ke mata tasiri cikin kunnuwa. Yaren da taji yana mata wani dadi,yana mata kuma kamanceceniya da yaren fullatanci,saidai yafi fulatancin tsari da dadi a kunnuwanta. Cikin girmamawa daya daga cikin mutanen dake sanye da suit dinnan ya bude masa murfin rolls Royce din yaja da baya da girmamawa. Saidai kuma ya waiwayo gefansa,inda take tsage zuciyarta da kwanyarta suna zurfi da nisa a tunani. "Bismillah" Yace da ita yana sake bude mata murfin sosai da wani yanayi da taji ya saukar mata da wani izza da girma. Kowa ya dakata.....komai ya tsaya saboda jiran shigarta mota kawai?,.....kamar a masarautarta ta agadez inda akasan tarin girma da kimarta?. A hankali ta taka da yanayin takunnan nata dake cakude da qasaita,ta taka motar tana shiga a nutse,ya tsugunna a hankali yana gyara mata abayarta data fito waje,muryarsa da taushi yace. "Kiyi addu'a......koda bismillah ce" Sannan ya maida murfin ya rufe mata. Ta cikin glass na window din ta bishi da kallo,sanda yake zagayawa zuwa daya side din,da dan murmushi kadan saman fuskarsa yana magana da balaraben. Ta cikin motar taci gaba da monitoring komai.....motsinsa da yadda yaci gaba da magana dasu. Yadda suke magana dashi cikin girmamawa da qanqan da kai......yadda yake magana dasu da wani yanayi......yanayin da yafi mata kama da yanayin mutumin da ya saba da iko tun daga haihuwarsa. "Ya salam......wayeshi?" Ta fadi wannan karon a sarari tana jin shakka da kokwanto suna cikata a kanshi. "Ina buqatar na sani......dole,ba malami bane kawai.....wannan fuskar da muke gani a agadez ba ita bace ta gaske.....wannan mutumin......bashi bane na gaske" Ta fadiwa kanta tana jin qwarin gwiwa. Tana jin zuciyarta na tunzurata......tana jin ya zama dole tayi bincike a kansa. Sanda take rubuta gajeran saqon tana aikewa,ta dauka zataji tsoro......ta dauka zataji tsoro game dashi ya kamata......amma maimakon wannan wani aminci da nutsuwa takeji. Ta tabbatar sultane bazai aminta har haka da mutumin da ba gaskiya a tare dashi ba,amma duk da haka......tanaso ta sani......tana buqatar sanin koshi waye.......koda ba dogon zama zasuyi ba......amma tana buqatar ta sani. *zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 08187255862 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 08187255862 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽LU'U LU'U (The diamond)💎 HUGUMA BOOK 03///PAGE 23 Cikin awa daya da mintunan qalilan suka qaraso. Babban hotel dake dab da harami wato raffle makka palace.Ta sake daga idanunta tana daban hotel din. Daya daga cikin hotel din data saba sauka duk sanda zataje umara. Yana mata dadi,yanayin tsari tsaro kulawa dama komai nashi dabanne. Hotel ne na masu iko.....sarauta sama hannu da shuni a kowanne bangare na duniya."Raffle?" Ta sake nanatawa wani mamaki me girma da nauyi yana danne zuciyarta,zatonta da zarginta kuma a kansa yana sake ninkuwa. Fuskarsu cike da alamu na sanayya, tashi fuskar kuma a sake da wani irin yanayi dake nuna nutsuwar da Allah ya yiwa ruhinsa baiwa da ita.Direct suka zarce zuwa elevator da zai rage musu tsahon tafiyar. Ko a ciki numfashi take ja kadan kadan tana sake satar kallonsa. So take taga wani abu daya sauya a tattare dashi amma babu. Shidinne dai......sheikh muhammad haisam din da suka taho tare daga agadez har zuwa makka din. Ba wani reaction nasa daya sauya, kamar komai yana kan muhallinsa ne, kamar ba wani baqon abu cikin lamarinsa, kamar dai normal daily life style dinsa kenan.A hankali elevator din ya tsaya, still bai kalleta ba, ya taka a hankali yana miqa mata hannunsa. Tsaiwa cak tayi tana duban lallausan tafin hannunsa daya miqa mata, idanunsa kuma suna kan wayarsa, da alama koda hannu daya koda hannayensa biyu dukka ya qware wajen sarrafa waya. Tafin hannun take kalla sosai, a karon farko taji wani tafi jinsa cikin nata hannun maimakon... Wannan rayuwar.....ba irin ta talaka bace" Ta fada a zuciyarta,saidai har a fili ta gaza mallakar kanta. Tsoro ne yake kamata zuwa yanzu,tsoron da yafi na dazu qarfi.Shurun da yaji ya sanyashi daga idanunsa ya zube a kanta,take idanuwansu suka gauraye da juna. Ya dan zuba mata ido yanason karantar abinda yake cikin ranta,amma saita kawar da kanta tana jin tsoro da shakkarta suna qaruwa."Muje?" Ya fadi a tausashe yana maida hannun nasa cikin aljihun jubah dinsa maimakon ci gaba da miqa mata shi.A nutse take biye dashi tana sake karantar sa takunsa. QASAITA kowanne motsi nasa nunawa zallarta. Hankalinta ya sake rarrabu Sashen da suke nufa.....bata taba sauka a wani bangaren ba,wannan block din ma bata taba hauroshi ba.Bullowar wani balaraben matashi ya sanyata janye hankalinta kadan. Kaman sauran ma'a... kammala ibadarta ta wuce.Bakin qawatacciyar qofar ya taka,ya matso da executive access card dinshi jikin qofar,tayi 'yar qaramar qara ta bude kanta da kantaIdanu akhnan ta sauke a hankali akan card din,adon gold din dake jikinsa na dabanne. Wani irin minimal design me daukan hankali. Ta aza idanunta akan embossed name din dake jikiAlsaamit shine sunan dake rubuce a jiki,akwai wani tiny emblem a jiki. Qawataccen crown me jan hankali sosai da daukan idanu.Tura qofar yayi,ya soma takawa zuwa ciki.Saita tsaya cak, qafafunta kamar sun qi motsi Cikin iikinsa yaji bata biye dashi,ya tsaya da tawa ya waiwayo da manyan fararen idanun sa yana dubanta.In salon bada sassauqan umarni. Shima nasa fararen idanun ya zuba mata,sannan ya sauke numfashi a hankali yana maida wayarsa aljihu still bai dauke idanunsa daga kanta ba."Ki shigo" Ya fada da wani irin coolness yanayinsa yana nuna hankalinsa kwance yayi maganar.Ci gaba tayi da duban labbansa ba tare data iya kallon qwayar idanunsa ba. Haka kawai taji qwalla tana cika mata idanu,saita motsa labbanta a hankali."Ban tambayeka shiga ba.....waye kai?" Ta sake fada har ga Allah tana jin tsoro duk da ta sani tana amintaccen muhallin da ba kamarsa duk duniya. Amma ta sani,duka wannan.......dan wadannan,tsarin tafiyarsu.....private jet......wannan suit din duka ba aikin sultane bane. Tasan kudin da zasu sauka da farko,tasan jirgin da zasu bi duka ta bakin shehnaz......amma a yanzu sabanin komai take gani.Idanma sultane ne.....tun daga private jet zuwa wajen girmamawa tarba da karramawa ma'aikatan hotel fa?."Ba gurin tsaiwa kiyimin tambayoyi bane nan" Sai ya daga hannunsa yana mata nuni da ciki kamar yana mata magana ne cikin ikon dake cakude da nutsuwa."Ki shigo" Ya rufe da fadin hakan cikin nutsuwar nan tasa.A hankali taji qafafunta suna saki,ta soma motsawa tana takowa zuwa ciki.A nutse ya saka hannu ya maida qofar ya rufe,sannan ya soma bin bayanta a hankali. Cak ta tsaya sanda yake tsaiwa Shima"Me yasa na yarda na shigo?,me yasa bance ba?" Ta tuhumi kanta. Saita daga blue eyes da sauri ta waiwaya tana sake dubansa."Ka fara bani amsa.....waye kai?". Idanu ya sake zube mata kawai yana karantarta ta cikin nutsuwa,tsoro,karaya duka yau yake... da sauri ta waiwaya tana sake dubansa."Ka fara bani amsa.....waye kai?". Idanu ya sake zube mata kawai yana karantarta ta cikin idanunta. Rauni, tsoro, karaya duka yau yake gani cakude cikin shudin idanun gimbiyar agadez din a yau. Kafaffiyar gimbiyar nan wadda ta bawa maza da yawa kashi......kafaffiyar gimbiyar nan wadda bata sauka daga kan ra'ayinta......kafaffiyar gimbiyar nan da batasan tsoro ko sauya tsari ba.Lumshe mata idanun yayi yana budesu a lokaci guda, wani abu daya sake bayyanar da zanuun kyanshi."Zan baki amsa" Sai ya dakata."Amma ba yanzu ba" Ya cikashe maganarsa."Sai yaushe?" Ta sake fadi da alamu wannan dabi'ar tata ta kafiya ta motsa. kanta,ya tara takawa a nankali yana nufar daya daga cikin qofofin dake cikin luxury living room din,ya budeta a nutse,ba tare daya kalleta ba yace."Ga dakinki.....ki shiga ki huta,ki kuma shirya nan da awa daya zamu shiga haram". Daga haka ya juya a nutse yana sake bude daya qofar dakin,ya taka a nutse yana shigewa ciki.Wannan mutumin?... meye ainihinsa?,Sheikh? businessman?,royalty?,Ko dukka?toh fa......masu karatu.....a samu wani ya taimaki akhnan ya bata satar amsa......ya gaya prince ne.....dan sarkin Ethiopia da kansa k tunani da canki canki ya qarasa zautata 😂😂😂muje zuwa mutane na💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 24* Sai taji kaman tana neman zama wani abu na daban. Yawan magana da kan kanta ita daya......yiwa kanta da kanta tambaya.......da yawan tuhume tuhumen da takeyi yiwa kanta duk ita daya,nema yake ya zame mata al'ada ko kuma dabi'a. Qafafunta a sanyaye ta taka zuwa qofar daya bude matan,ta tura a hankali tana saka qafafunta saman lallausan luxury carpet din dake malale cikin dakin. Idanunta ta ware tana kallon dakin da kyau. Wani irin tsari ne me daukan hankali sosai,wani irin yanayi me sanyi da saukarwa zuciya dama gangar jiki nutsuwa. Idanunta suka sauka a bangon gabas na dakin. Glass ne gaba daya ta gurin,glass din da aka qawata da manyan curtains na alfarma masu kyau. Samu kanta tayi da takawa zuwa gurin,tana jin kamar ana jan zuciyarta. Tana jin kamar akwai abinda yake fusgarta zuwa gurin cikin wani irin yanayi. Tayi tsaye gaban labulen,zuciyarta da qirjinta suna bugawa da wani yanayi na daban. Yau zataga wannan view din......wannan ganin da take kwadayi kai tsaye daga masaukinka cikin raffles makkah palace din. Ta miqa hannunta a hankali,ta yaye curtain din,take cikakken gani daga harabar harami dukkaninta ta bayyana kamar tana tsaye cikin gurin. Wani bugun zuciya me cike da nutsuwa ya sakata lumshe idanunta sannan ta budesu. Wani irin yanayi me nutsuwa ya saukar mata,daidai lokacin,kamar ladanin masallacin haramin sheikh Ali Ahmad mulla yasan tana tsaye ne.....a daidai lokacin zuciyarta tana lilo da wani irin yanayi ya fara kwararo kiran sallan isha'i.....kiran sallar da taushinsa da yanayin sautinsa mai ratsa gabbai ya sanyata zamewa a hankali saman gwiwoyinta ta zauna sosai saman abun sallar tana sauraren kiran har zuwa sanda ya kammala. Haka kawai bawai don ta sani ba ta samu kanta da daga hannuwanta tana addu'a. Tana addu'a wa sultane.....tana addu'a masa ingantacciyar rayuwa me tsaho,sai data qarar da dukka addu'arta a kansa ba tare da tasan ita me zata roqarwa kanta ba. "Ki shirya.....zamu shiga haram" Ta tuna maganarsa. Dan turus tayi bayan data laluba,ta tuna bataga birra ba tunda suka taso,bataga falaak bama. To bama falaak ne damuwarta ba,birran ce. Ta yaya zata iya hadawa kanta ruwan wanka?,ta fidda kayan da zata sanya ta kuma shirya kanta da kanta?. Tayi turus tana qiyasta yadda zatayi komai din da kanta,karo na farko a rayuwarta kenan. Har cikin ranta taji ta takura,har cikin zuciyarta taji kaman ba zata iya ba,amma data tabbatar ba birra a kusa.....babu kuma wani sauran hadima daya rage da zata taimaka mata,dole ta soma rage kayan jikin nata,sannan ta daura towel babba ta wuce zuwa toilet din. Banda tazara da suke dan bayarwa tsakanin kiran sallah da iqama ta sani tabbas saita makara. Tun a iya gurin hada ruwan wanka kawai ta fahimci batasan komai ba,bata kuma iya komai don taimakawa kanta ba. Da farko ta hada ruwan da zafi,sai data fita ta sake gyarawa,sai kuma ta salamtar da ruwan gaba daya. Tayi wankanne kawai ba tare da ruwan ya mata daidai da yadda birra ke hada mata ba,sannan ta fito ta fara kici kicin tsane jikinta da shafa mai. Wannan bata dauki lokaci ba tunda ta saba,saidai gurin gyara gashinta wanda daga qarshe sakin gashin kawai tayi ta soma neman wanne kaya zata saka. Turus tayi tana duban ma'ajiyar kayan da kafin su haura saman har cikin ma'aikatan dake tiri tiri da baqi ta gama shirya mata su tsaf a cikin gurin. Hannu tasa tana duba kayan daya bayan daya,ranta ya baci,taja qaramin tsaki. Wanne irin shirin kaya birra tayi mata?,bataga under wears ba banda guda daya. Ba rigar bacci sai guda daya qwal......bata saka mata kayayyaki da yawa ba daya kamata ace suna cikin kayanta,kayan da da yawa birran ce take da alhakin hadasu,ta kuma saba,ya zame mata jiki,don ko tafiya tsakanin agadez da Niamey da takeyi a baya duk qarshen sati birran ce ki shiryawa da tsara komai,ba'a kuma taba samun akasi ba,to a yanzu batasan sanadin wannan mantuwar ba. Hakanan ta zaro daya daga cikin abayas din da sukafi yawa a kayan nata. Sakakkiya ce sosai,wadda bata nuna shape dinta kwata kwata. Saidai kuma yadin wani irin yadin silk ne me asalin tsada dake wata irin walqiya yana sauya launi. Duk da maroon ce amma idan haske ya haska wani gurin a maimakon maroon din sai ya koma kaman baqi. Wani irin mugun kyau da dacewa da launin fatarta tayi,wani irin ado ke jikin abayar da shi kadai zai gaya maka tsadarta. Gashinta kawai ya rage ta daureshi,saidai tayi iyakar yinta ta kasa,har tsintsiyar hannunta tana riqewa saboda yadda tayita kokawar tajeshi ta matseshi yadda birra ke mata. Tilas ta sakeshi tana yarfa hannu kaman zata saki kuka. Bata saba ba,ba ita kewa kanta ba kuma zata iya ba,dole ta jawo Malaysian hijab baqi da yazo maqale da abayan,wanda bayansa yafi ko ina tsaho a jikinsa ta zura,take wannan kyakkyawar fuska ta fito sosai da wani irin haske me jan hankali ta tsakanin fuskar hijab din. Tana zura wani designer snickers taji ana knocking a tausashe. Ta qarasa saka takalmin tana jin yadda ta gaji gaba daya sannan ta miqe tana nufar qofar. KAMSHINSA.....shine abu na farko daya fara marabtarta.....qamshinsa dinnan data gama aminta shine JARRABAWARTA a tattare dashi.....jarrabawar da take fatan ta zama ita daya ce inde a tare dashi ne......kada ta kasance me abokiyar tafiya. A nutse ta daga blue eyes dinnan nata tana saukewa a kansa. Yana tsaye gaban kyakkyawan fridge din yana tsiyaya ruwa me madaidaicin sanyi cikin glass cup din daya dora saman fridge din. Idan tace bataji zuciyarta tayi rawa ba a lokacin ta sani.......tabbas ta gunduma qarya.......ya fita sosai a GIANT dinsa......tsaho da kaurinsa da murdewar muscles dinsa da suka bayyana ta hanyar kafadarsa guda daya dake waje. Komai nasa fari qal......a yau da yake sanye cikin ihram komai nasa ya canza. Wani irin sanyi....wani irin nutsuwa da wata irin kwarjini ta cikin fuskarsa dake nuna zallar nutsuwa da muhimmancin ibadar da ya dauki niyya. A hankali take tana qafafuwanta.......kafin ta samu kanta da tsaiwa cak tana kasa ci gaba da daga qafarta. Yau din kamar an sauyashi,ainihin tsarin halittarsa tana cika idanunta. Ya mata wani irin kwarjini daya daki zuciyarta. Ba luxury......ba jubah......ba cloak thobe......sai lallausan qamshinsa da a yau takejin ya qara taushi kamar an surkashi da wani abu daban. Fari kawai.....tsarki kawai.....nutsuwa kawai.....sai taji wani abu ya motsa zuciyarta. "Me yasa yafi kyau a haka?" Ta tambayi kanta kafin zuciyata kwabeta,ta kuma tattara komai ta watsashi a gefe. Daidai sanda ya kammala shan ruwan,ya ajiye cup din ya juyo da nutsuwa sai idanunsa suka sauka a kanta. Ta bada baya ne.....wannan ya bashi daman ganin doguwar sumarta me sulbi data jera tsaho da tsahon hijabin jikinta. Idanunsa ya lumshe sannan ya bude,yana jin Allah ya taimakeshi daya gani,inda bai gani ba a haka zata fita......a haka zata ratsa mutanen da basu da qayadadden adadi. "Akhnan...." Ya kirata a karon farko da wani irin sautin daya sanyata taji wani abu yana ratsa qashin da qafafuwanta gaba daya. Waiwayowa tayi tana dubansa ba tare data iya sake takawa ko motsawa ba,saboda har cikin b'argonta kiran ya kutsa yana ajiye mata wani yanayi a dukka sassan jikinta. Takowa yaci gaba dayi ba tare daya dauke idanunsa daga saman lips dinta ba,lips din da sai yau yaga ainihin color dinsu. Wai irin glowing suke,sirara dasu wanda ko baka taba ba kasan zasuyi laushi sosai. Dab da ita ya tsaya,ya kuma zura hannunsa ta bayan hijab din a hankali yana kama gashin. Gashin da ya masa wani irin santsi a hannu har yasa tsigar jikinsa tashi. "Ki rufe" Ya fada yana zare hannun nasa a hankali. "Ban iya ba" Ta fada a wani mugun narke kamar qaramin yaron dake jin rigima. Yanayin ya sanyashi tsaiwa cak.......sannan ya zuba mata idanu yana jin wani abu yana sauka a sassan jikinsa. Tayi maganan ne har ga Allah kuma kanta tsaye,saboda wani mugun gajiya da takeji hannuwanta sunyi,ta kuma sani,babu ta yadda zata iya taje kan nan ta daureshi koda shigen yadda birra take mata ne ballantana irinsa. Batasan tone dinta ko mode dinta ya sauya zuwa kalan shagwaba ba.....shagwabar da sultane da mammina kawai take yiwa ita. Gefe guda har yanzu tana masa wannan kallon.....wannan kallon tuhumar....wannan kallon rashin amincin....wannan kallon na waye kai?....wannan kallon na ban aminta dakai ba. Numfashinsa ya dinga zarowa daga tsakiyar qirjinsa da qyar kamar wanda aka saka wani abu aka matse masa shi. Yau yaga wani side......wani side da yake mutuwan so tattare da mace. SHAGWABA the only thing daya fara banbanta halittar mace data namiji kenan. Baice mata komai ba sai taga ya juya yana komawa dakinsa,bai kuma dauki lokaci ba ya fito hannunsa dauke da wani comb. Ajiyewa yayi,ya daga manyan fararen idanunsa yana kallonta. "Essaie un peu" Ya furta a nutse yana sanya idanunsa cikin nata. A hankali ta zare idanunta tana jin wani iri,kasheta yakeyi.....kasheta yakeyi da wani irin emotions a duk sanda yayi mata magana da French,tana jin kamar a bakinsa aka halicci yaren.....tana tsoro ta jarabtu da son yaren a bakinsa kamar yadda turarensa ya zame mata jarrabawarta. Cikin zuciyarta take ayyana ta yadda zata zare hijabin a gabansa......amma kafin takai qarshen tunanin sai taga ya juya a nutse yana tattakawa zai fice. "Me yasa yake hukunci da wuri?" Ta tambayi kanta. Kamar fa yanzu ita takeson space,ya bata space din kuma me yasa takejin wani iri?. "Sai ya jira.....ya jira na fada masa ya fita mana" Ta fadiwa kanta da kanta,saita samu kanta da hararar qofar daya fice din. Hijabin ta zare,sannan ta dauki comb din ta soma gwada tajewar. Bashi da tauri sosai,amma yana da tsaho sosai da cika,don idan ta wareshi duka zai maka wahala kaga fuskarta. Jefar da comb din tayi saboda da gaske ta gaji,ta dakata tana maida numfashi kafin ta soma hade sumar,saidai sau uku tana hadewa yana wargajewa,sai kawai taji kuka yana zuwarmata,ta saki gashin tana zama saman stool din dake dab da conceal mirror din dake gurin. A nutse ya buda qofar yana shigowa,idanunsa suka sauka a kanta sanda take dora tafin hannunta tana rufe fuskarta dasu. Kukanta wani private abune da ba kowa take bari ya kalla ba,taji kuma shigowarsa,bataso kuma yaga hawayenta. Gajiya takeji yau daya da duk wata hidima,bata saba ba,ba ita takewa kanta ba. Kamar ya fahimci hakan,sai ya tako a hankali yana zaro wayarsa dake aljihunsa. Kadan yayi danne danne sannan yayi kira ya kara a kunnensa. "Ishee ergi" Ya fada a taqaice sannan ya maida wayar aljihunsa. A nutse tsaf ya zauna yana qare mata kallo. Dole saita boye rauninta.....dole saita bayyana qarfinta da jarumtarta,bayan rauninta a bayyane yake. Murmushi kadan ya subuce masa sanda yake tunawa. Ranar da zai cewa nanay dinsa ga jinin safeena dinta......ranar da zai cewa nanay safeena tabar tsatsonta har uku a duniya. Tunaninsa ya yanke saboda izinin shigowa da ake nema daga waje,sai ya miqe yana takawa zuwa bakin qofar ya bude. Birran ce.....birran da yace a turota,taja baya cikin girmamawa ta rusuna tana gaidashi. "Kuyi saurin fitowa lokaci ya kusa qurewa" Ya fada yana fita a dakin. "Allah ya taimakeki" Birra ta fada murmushi na fita saman fuskarta. A duniya wani irin farinciki takeji ida taganta tare da sheikh haisam. Wani dadi takeji idan taga rayuwarta daure data sheikh haisam din. Saboda abune sananne ga duk masoyinta......tayi tsintuwar wani kebantaccen LU'U LU'U ne me girman darajar da har yanzu me yiwuwa bata ganeshi ba. Tana zaton iya TAGULLA ne kawai yasashe mara daraja.💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 25* Da sauri ta sauke hannunta,ta kuma jefawa birra harara da jiqaqqun idanunta. Kafin tace komai birra tayi qasa da kanta. "Don Allah kiyi haquri,ba laifina bane,yallabai ne ya tsara tafiyar kowa da masaukin ya zama daban daban.....muna qarqashin kulawar yaranshi" "Yaranshi?" Ta furta tana duban birra. Kaman zata sake cewa wani abu da ita sai kuma tayi shuru tana dauke kanta miskilancin ya motsa,wannan ya bawa birra daman matsowa ta soma gyara mata gashin kamar yadda ta saba,wanda cikin minti biyu ta hade mata shi tsaf,ta kuma daureshi cikin madaidaicin ribbon,sannan ta miqa mata hijab din ta zura. "Ina falaak?" Ta tsinci kanta da tambayar birra. "Suna nasu hotel din a masaukinsu" Birran ta amsa mata. Mamaki kadan ya kama akhnan,wato ita hankalinta kwance?,yarinyar bata da hankali,haka kawai tabi wani namijin hankali kwance ba kuma wanda take nema?. A qasa ta sameshi har ya sauka zuwa babban reception na hotel din. ya kalleta sau daya saidai bai soma tafiya ba har sai da tazo dab dashi. A hankali suke takawa,cikin wani yanayi daya sanyawa zuciyarta nutsuwa. Iska me kyau....haske me haskaka zuciya dama gangar jiki.....kai kawo na mutane dake cike da nutsuwa da yanayi na ibada,bautar Allah cikin sakankancewa.....nutsuwar ruhi dama ta gangar jiki gaba daya. Wani abu ya sake daukar hankalinta yayin shigarsu haram. Kebantacciyar mashigar da tunda take zuwa bata taba shiga ta gurin ba,bisa jagorancin mutum ukun da suke sanye da uniform na ma'aikatan dake kula da haram baki daya. Tun takowarsu gurin suka iso su uku "Barka da zuwa sheikh" Suka fada cikin girmamawa. Murmushi ya saki a nutse,murmushin dake sake cika haibarsa da kamalarsa,yake sake fitar da sirrin kyansa. Sai ya miqa musu hannu sukayi musabaha. "Sheikh yasir addosary ya sanya hannu kan takardar zamanku......amma ba shine zai jagoranci sallar isha'i ba,sheikh abdurrahman assudais ne....saidai yana gurin,zasu dan zauna a tsakaninsu,lokacin kamar zai isa ka kammala umararka ku zauna dasu" Yayi maganan cikin harshen turanci wanda hakan ya bawa akhnan damar jin dukkan abinda ya fadi din. Maimaita maganan ta soma yi cikin kanta. Da waye zai gana?,da waye zaiyi meeting?. Imams na haram?......inde daidai taji imams na haram ne.......WAYESHI? Tambayar ta sake dokawa cikin kanta,saita daga kan nata da sauri tana ajewa a kansa,daidai sanda ya juya harshe yana bawa hadiman amsa da harshen larabci maimakon turancin da suka masa magana dashi. "Kuma?.....an kuma?" Ta furta a hankali tana jin wani tsoro nasa da mamakinsa yana kamata. "Anya bame had'ari bane?" Ta sake tambayar kanta tana jin tana rikicewa kadan. Yare nawa ya iya?,harshe nawa yake iya sarrafawa. Da farko yana hausa duk da bata zauna a bakinsa sosai ba ta yadda idan yanayi saika gane ba yarensa bace.....English.......france..... Tuareg kadan kadan.....ga kuma larabcin da bata jin komai a cikinsa......a iya haka ya tsaya?,ko da ragowar yaruka?.....WAYESHI.......tabbas akwai wani lullubi cikin rayuwarsa......akwai abinda dukkaninsu basu sani ba,ita da sultane dama dukkan wanda yake tare dasu. ME YAKE BOYEWA?,Mene manufofinsa?,ta samu kanta da fada tana jin yadda larabcin ke fita tartar daga bakinsa,bashi da maraba da Accent na larabawan da suke musu jagora. Hanya kawai taga ana buda musu duk da yawan mutanen dake gurin,suna sake gaba.....suna kusantar inda duk zuwanta bata samun daman isa gurin. "Ta wannan hanyar sheikh" Jami'in ya sake fadi yana musu nuni da wata kebantacciyar hanya. Cikin mintuna qalilan suka iso wani guri,kebantaccen gurin da bata taba zata za'a sameshi a guri me cike da cunkoson al'umma haka ba. A tsare yake,ba cunkoson mutane,sai shimfidu bisa tsari da tarin tsaro. "VIP zone sheikh zamu qarasa" Ya sake fadi cikin girmamawa ganin ya danyi slow kadan da tafiyarsa. "Ki jira a nan.....kiyi sallarki a nan" Ya fada a nutse sannan ya juya yana takawa jami'an suna biye dashi ta wata hanyar da take dab da inda zai kaika bakin ka'aba matsayar da liman yake tsayawa a duk sanda za'ayi sallah. A hankali ta taka zuwa saman shimfidun. Tana duban matan dake zaune cikin nutsuwa samansu. Dukkaninsu kusan qabilu ne daban daban daga qasashe daban daban,saikin lura da gaske zaki gane banbancin yanayinsu,alamu kadan tasa ta iya gane daga gidan mulki ko sarauta suka fito suma. Nutsuwarsu da shigarsu ta daban ce. "Ga guri nan" Taji wata sassanyan murya tayi magana daga bayanta. Hausar da taji ya sanyata waiwayawa da sauri tana neman me maganar. Kyakkyawar matashiya ce,wadda aqalla zasuyi sa'annin juna ita da ita a qiyasin shekaru nakai tsaye datayi mata. Murmushi ta sakar mata tana sake nuna mata muhallin dake kusa da ita wanda babu kowa. A hankali ta tsinci kanta da maida mata murmushin,sannan ta soma takawa zuwa inda tayi mata tayin,ta zare takalminta a nutse tana hawa saman carpet din. Samun kanta tayi dayin bismillah kafin ta zauna,abinda ya tsaye mata cikin zuciya. "Yaushe kika fara koya?" Ta tambayi kanta,bata da amsa bata sani ba,kawai ta samu kanta dayi ne. "Halan ke dayace kema.....ba abokan tafiya?" Matashiyar ta sake fadi tana murmushi da alamun dake nuna yawan murmushi yana cikin dabi'arta. Kai akhnan ta daga mata a hankali tana qoqarin sake aza murmushi akan fuskarta. "Ni ni dame gidana ne......yana bangaren maza.... Kefa?" Tambayar sai ta yiwa akhnan nauyi,ita dawa zatace mata?. "Ni sunana ameenatu muhammad jadda.....amma ana kirana da iffa......kefa?" Sosai sunan ya yiwa akhnan dadi,sannan kuma sai takejin kamar akwai inda ta taba jin sunan. "Khadeeja muhammad hammud" Ta amsata a taqaice. Kai iffa ta jinjina "Sunanki yayimin dadi.....daga nigeria nake......kekam nasan ba 'yar can bane....." Kai ta gyada a hankali murmushi yana sake subuce mata kadan. Karon farko da hira da wani ya burgeta,wanin da ba shehnaz ko aisa ba. "Nijer.....agadez" Idanu iffa ta fidda kadan. "Daga agadez palace?" Kai akhnan ta gyada a nutse "Yeah........haba,kaman nasan sunan......daughter of sultane muhammad hammud.....right?" Iffa ta furta tana dan fidda idanunta waje tana nuna akhnan da yatsa. Wannan karon dole murmushin akhnan ya sake qaruwa,ta sake daga mata kai a hankali,saidai tayar da iqama da aka fara qoqarin yi shine abinda ya katse wannan hirar tsakaninsu. Cikin sahu da matsayin da Allah ke bawa bayin da suka samu daman yin sallah a gurin suka gabatar da sallar isha'i ta wannan rana. Sallar da suna sallameta basu samu daman yin wata maganar da iffa ba me gidanta ya kirata "Save my number please prince khadeeja" Iffa ta fada tana murmushi. A nutse ta fidda wayarta ta karantawa akhnan numbers dinta ta dora da fadin. "A swissotel muka sauka....zamu qara kwana bakwai kafin mu wuce,ina fatan zamu sake haduwa?" "In sha Allah" Akhnan ta amsa mata. Tana jin kamar ta samu wani madadi,wani madadi nasu shehnaz da aisa data baro a agadez din. (One of jadda's family......sabreen namesake). Duk da yawan mutanen dake kaiwa da kawowa amma hakan bai hana idanunta ganinsa ba. Daga nesa sanda yake takowa sanye da wannan farin ihram din data kyawun daya masa ya kasa dusashewa a idanunta da zuciyarta. Daga nesa kadan take hangensa,hannunsa cikin na sheikh abdurrahman assudais,gefansa kuma sheikh yasir aldosary. Dukkansu suna murmushi ne,da alama akwai magana me muhimmanci da sukeyi. Hanya ce da idan zasu wuce ake cikata da security,suna kuma wucewa ne da dan sassarfa saboda mutane masu daukan hoto da kuma masu son tsaidasu. Ta lumshe idanunta tana sauke ajiyar zuciya don ragewa zuciyartata nauyi. Tantama shakka da kuma kokwanto a kansa sake cikata yakeyi. Da gasken gaske takeson sanin shi waye,ta kuma fara aika bayani a kansa......amma tana jin kamar amsar ba zatazo mata a sanda takeso ba. Ta sake daga idanunta,sai ta hangeshi yana takowa da wani irin nutsuwa,haske ihram din jikinsa yana sake haske fuskar nan tasa data rasa wanne irin sirri ne kwance a cikinta. Sirrin da idan ka kalleta kwarjini nutsuwa da kamala sune abinda kawai zaka iya gani. Da alama bai ganta ba,wannan ya bata daman sake shigewa mutane kadan tana kallonsa,tanaso taga ta yadda zai iya zaqulota,duk da tare suke da daya daga cikin askar na gurin suna magana kadan kadan. Sallama sukayi ya koma bakin aikinsa,shi kuma ya tsaya cak da alamun yana wara idanunsa ne don zaqulota. Idanunta zube fes a kansa,ya danyi qasa da kansa kamar me kallon wani abu,sai kuma ya juyo cikin second daya saiga idanunsa cikin nata. Zare idanun nata tayi,tana jin alamun takunsa a jikinta,tana jin sanda ya iso dab da ita,tana jin muryar nan tasa me zurfi da wani kwarjini yana fadin. "Ina fata kin dauki niyya?" Kai ta daga a hankali,sai ya juya yana fadin. "Bismillah" Biye take dashi a hankali,qafafuwansu suna sake musu jagoranci zuwa gaban ka'aba. Idanunta akan dakin,daki mafi tsarki,muhallin da yafi kowanne martaba tsarki da daukaka a duniya. Tana sake kusantarta tana jin yadda zuciyarta ke sake sanyi.....tana qara duka taku guda tana jin yadda nauyin dake saman zuciyarta yana raguwa. Sanda ta tsaya a saitin inda zasu fara dawafi,girman dakin ya bayyana a gabanta,sai taji wani karayar zuciya. Ta sauke idanunta akan tarin mutanen dake dawafi a sannan. Yau din kamar akwai cikowar jama'a sosai,abinda tafi tsoro kenan yafi kuma bata wahala duk cikin umara ko aikin hajji,wannan turmutsutsun,wannan cikowar. Takawa ya fara yi,tana daga gefansa,a hankali take ajiye takunta duk inda ya ajiye nasa,suka fara zagayen farko. Dukkaninsu zuciyoyinsu sunyi nisa wajen addu'o'i da jin kusanci da mahaliccinsu. Ta lumshe idanunta,tana jin yadda cunkuso yake qara daduwa,amma hakan bai hanata jin daddadan sautinsa ba. Sautinsa shi kadai yana fita da wata irin nutsuwa,sautinsa shi kadai duk da tarin muryoyin bayi dake cike da roqo da kuma fata kala daban daban,saidai batasan dalilin daya sanya kunnuwanta ke tsame iya nasa sautin kawai ba. Wani buri ne da takejin a yau ya ninka yadda ta saba jinsa cikin zuciyarta.....burin kaiwa gaban ginin dakin ka'aba,ta sanya hannunta ta tabashi,ta kifa fuskarta a jiki tayi kuka ta kuma gayawa Allah buqatunta. Tunda take zuwa bata taba damuwa da yin hakan ba,hasalima yawan cunkuson shike firgitata,tafi zabar yin dawafinta a sama tayi ta kammala,amma a yau din sai takejin shine abu guda dayan da take buri wato ta isa ga ginin dakin ka'aba. Tanajin kamar buqatunta masu nauyi ne a wannan karon......tana jin kamar buqatunta sun rinjayi na kowanne lokaci. Wannan qawa zucin ya sanyata ta fara neman hanyar kutsawa ta tsakanin wani rukunin 'yan qasar Malaysia da alamu ke nuna ahali daya ne,saidai yadda suka matseta a cikinsu ya sanya numfashinta ya soma sama sama.💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 26* "H.....ha.....haisammmm" Ta fada da sauri tana qoqarin qwato numfashinta. Har tsakiyar kansa yaji saukar sunan cikin kunnuwashi da wani kebantaccen yanahi,wani baqon sauti da a yau ya fara jin fitar sunan a gurbin. Da wani irin Zafin nama ya miqa hannunsa ya damqe nata,sannan ya jawota daidai kafadarsa yana manne tafin hannunsa cikin nata da wannan yanayin dake zare mata kowacce laka ta jikinta ya maye gurbinsa da kasala. Sosai ya mata gurbi kusa dashi,ya hade dukka tazarar dake tsakaninsu ta yadda ko zare bazai iya ratsawa ba. Idanunta ta daga tana qoqarin kallon fuskarsa. Zafin naman daya gwada mata kadai ya isa ya gaya mata qarfi da kuzarin daya mallaka. Ba ita yake kalla ba,idanunsa suna gabansa da yana lissafa yadda zasu samu isa gaban ka'aba cikin sauqi. Sai sautin sunansa daya fita a bakinta da yaketa maimaituwa cikin kanshi. "Ki zauna kusa dani" Ya furta cikin wani salo na umarni kai tsaye. Ya fahimci abinda yasa aka matseta har haka,ya sani kuma a daidai wannan lokacin bata da qarfin da zata iyakai kanta gaban ka'aba din. Da sauri ta sauke idanunta daga kansa zuwa qasa,zuciyarta ta soma motsawa. "Ya Allah......" Ta fada tana jin wani faduwar gaba tana samunta. Me ya kamata ta fara roqa?wacce addu'a zatayi?. Kamar yasan tambayar dake ranta kenan,wannan muryar tasa ta sake shiga kunnuwanta da wasu addu'o'i da taji zuciyarta na kwanciya kaman an yayyafa mata ruwan sanyi,sai kawai ta dinga maimaita abinda yake fadi. A duk sanda ta maimaita fadin kowanne harafi dake fita a bakinsa sai taji zuciyarta ta sake nutsuwa. Duk sanda ta maimaita sai taji wani irin nutsuwa da kwanciyar hankali. Abu daya data ga yanayi,sauya mata bangare wanda batasan adadin sau nawa yayi ba. Daga kafadar hagunsa zuwa ta dama,daga kuma kafadar damansa zuwa hagu. Wani irin kariya takeji tako ina.....wani irin aminci da tsaro irin wanda bata taba jinsa ba tunda take zuwa umara,koda kuwa da hadimai guda nawa zatazo. Bata sake jin an matseta ba tun matsewar farko,bata sake maimaita kowacce addu'a ba sai addu'o'in da suke fita daga bakinsa cike da wata irin nutsuwa,addu'o'in da koda batasan ma'anarsu ba......amma tana jin wani gamsuwa da aminci a cikin maimaitasu. Zagaye bakwai me cike da wani irin yanayi.....zagaye bakwai me cike da wani sirrin aminci da nutsuwa da bata taba sanin akwai irinsa ba. Suka tsaya cak,tsill hannunsa cikin nata. Akwai rangwamen cunkos zuwa sannan,saidai hakan bai hana cunkuson masu son zuwa gaban ka'aba. Hannunta ya saki a hankali,sai ya riqe tsintsiyar hannunta yana zagayo da ita gabansa. Qugunta ya riqe da hannunsa guda daya,a hankali ya sanya idanunsa cikin nata,sai itama ta daga blue eyes dinta tana ajesu a nasa. Wani irin abu ya sauka saman zuciyar kowannensu,wani abu me nauyi taji yana taba zuciyarta da wani irin yanayi data gaza fassarashi. Kallon ido cikin ido da qaramar tazara irin wannan.....tazarar da hatta da numfashin junansu musayarsa sukeyi,tazarar da take iyajin yadda jikinsa yake gogar nata,tazarar da ta fara gaban babban daki.....babban gurin da babu irinsa,tazarar da ta sanya wata nutsuwa a ruhinta....wannan tazarar da taji a karo na farko ba wata tazara mai qaranci da muhimmanci irinta. "Es-tu prête?(kin shirya?)" Ya furta yana motsa labbansa da suka janye hankalin Akhnan sosai,sannan cikakkiyar girarsa guda daya tana dagewa sama. Sai data lumshe idanunta a hankali,tana jin wani yanayi na daban yana ratsata. Tayi qoqarin motsa labbanta amma ta gaza cewa komai,sai kai ta daga masa a hankali. Shima da idanu ya amsa mata,kallon daya sanya taji wani abu yana narkewa tun daga zuciyarta yana kwaranya a gangar jikinta gaba daya. Ba zato taji yasa hannuwansa biyu ya rabata da qasa. Tadan tsorata har batasan sanda ta riqe faffadar kafadarsa ba. Hannunta ya sauka saman lallausar fatar kafadarsa......laushinta ya hadu da taushin nata tafin hannun. Saman qafafunsa taji ya dora tafukan qafafunta bayan ya juyata,bayanta yana cikin qirjinsa,ya saka hannuwansa ya zagayesu saman cikinta,ya mata kyakkyawar garkuwa da dukkan jikinsa. Ta yadda ba wani abu da ya isa ya tabata.......a yanayin da ba wani abu da zai kusanceta muddin ba gangar jikinsa ba. Habarsa ya dora saman kafadarta,da wani kusanci sosai cikin muryarsa a tausashe yake fadin. "Zaki tafiya saman qafafuna....zamu qarasa gaban ka'aba kiyi addu'a.....gurine me muhimmanci sosai.....gurine na amsa addu'a da dukkan buqatu.......zakiyi alqawari?". Sauka kowacce kalma take daga bakinsa kai tsaye zuwa kowane sashe na jikinta,saqon da dukka maganar suna ratsata. Alqawari daya fada ya sanyata bude idanunta dake lumshe tunda ya fara maganan,bata motsa ba,amma yaga alamun bude idanun nata. "Zaki sakani cikin addu'arki?" Ya fadi maganan yana kaiwa qarshenta da wani irin numfashi me nauyi. Shuru kawai tayi.....tana jin sautin bugun zuciyarta ta cikin kunnuwanta. Zata sashi a addu'o'inta kamar yaya?,bata fahimta ba,ba kuma zata iya tambaya ba. Abu daya ta sani.....zai mata wani abu da zai shiga sahun tarihinta. "Kinyi alqawari?" Ya fada yana dan matsa qashin qugunta kadan ba tare da yasan yayi hakan ba. Kai ta daga a hankali ba tare data shiryawa hakan ba. Qafarsa ta farko ya cira,wani tsoro ya kamata taji kaman zata fadi,saita manne bayanta sosai da jikinsa tana riqe hannuwansa dake qugunta. "Ki tsaya" Ya sake fadi kaman me rada a hankali muryarsa na sauka da wani irin sanyi. "You're safe.......kina tare dani" Ya sake maimaitawa. Sai taji ta aminta dashi din.....ta aminta da maganarsa,sai taji ta saki jikinta hankali kwance. Yana takawa a hankali da ita,mutane na wucewa ta gefansu amma tana jin kamar komai ya tsaya. Da dukka jikinsa ya bata kariya,yana kutsawa da ita da wani irin qarfi na zuciya da hikima ba tare da cutar da kowa ba har suka isa gaban ka'abar. (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) Sauketa yayi a hankali daga saman qafafunsa,ta sake takawa ta matsa zuwa gaba,bai matsa daga bayanta ba,sai ya sanya hannuwansa ta gefe da gefan kafadunta yana dafe bangon ka'aba dashi,yayi mata wata ingarman rumfa da gangar jikinsa,ya lullube bayanta da kyau da jikinsa,ya kuma samar mata da space din da zai wadaceta tayi addu'a. Hannunta ta dora itama saitin nasa tana dafe ka'aban. A karon farko kenan,duk da shekarun data dauka tana zuwa. A karom farko ta sanadinsa,da dukka wata kariya da zai iya bata ya sadata da dakin. Sai taji wani hawaye me dumi yana saukar mata,ta masa a hankali ta sumbaci hajarul aswad,ya sake matsawa da ita gefe kadan,ta saka bakinta fa sumbaci ka'aban,kafin ta dauke kanta ya sake manneta cikin jikinsa,ya kuma zuro kansa ta kafadarta,abinda ya hanata iya dagowa kenan,sai tabar fuskarta a jikin dakin tana sauraren fitar numfashinsa,dumin jikinsa,da sautin addu'o'in da ba zata iya tantance abinda yake roqa ba. Wani yanayi ta jita a ciki,irin yanayin da yafi kowanne yanayi yi mata dadi cikin duniya. Ya zareta a hankali ya riqe qyam cikin jikinsa yana sake zareta daga turmutsitsin. Sallah sukayi raka'a biyu daga nesa kadan da ka'aba din. Saita samu kanta da cikar hawaye a idanunta. Ta daga hannuwanta ta rasa me zata roqa?. Bayan addu'a data sakewa sultane,a yau saita samu kanta da yiwa mamarta addu'a. "Ya Allah,kayi mata rahama.....ka shafe kurakuranta......ka yafe mata zunubanta Allah" Saita dakata,tana tuna me zata roqawa kanta. "Allah......ka......" Kasa qarasawa tayi,tana juya abinda zuciyarta ta raya mata ta roqa din,ya cancanta?,ya kamata ta roqi wannan kuwa?. Wannw tabbaci take dashi?,wanne yaqini take dashi?. Bata da dukkan wata makama......bata da dukkan wani qwarin gwiwa nayin addu'a akan wannan. Daga inda take zaune tana iya ganinsa. Tsaiwarsa a sallah......ruku'unsa dama sujjadarsa. Komai nasa sai take ganin yana da wani irin banbanci da wanda ta sani da kuma wanda ta saba gani. Yadda ya zauna saman qafafunsa,cikin wani tawali'u da qanqan dakai,ya hade dukka tafukan hannayensa,ba wani sauran izza a tare dashi.....ba wata qasaita....sai zallar nuna miqa wuya ga ubangiji,sai taji itama tata zuciyar tana karyewa. Kuka kawai taji tana son tayi,ba tare da tasan dalili ba,sai kawai ta cure guri daya,ta cusa kanta tsakanin cinyoyinta tana bawa hawayenta daman sauka yadda sukeso. Ta dauki mintuna aqalla ashirin a haka......a hankali taji kaman qamshinsa a kusa da ita.....a hankali takejin kamar akwai wani kusanci na daban a tare da ita,sai ta soma qoqarin daidaita kanta da sassauta kukan,kafin a hankali ta soma qoqarin daga kanta. Shine a zaune a gabanta,da wani irin coolness ya zuba mata manyan idanun nan nasa. Kallon ya mata nauyin da ba zata iya jura ba. "Kiyi addu'a......guri ne na bayyana dukkan damuwa da samun waraka". Sai ya miqe a hankali ba tare da yace komai ba. Maganar ta tsaya mata a rai,tayi qasa da kanta a hankali tana bawa zuciyarta daman ambatar dukkan abinda take buri da muradi. Karo na biyu ta sake ganin an miqa mata cup,ta daga idanunta a hankali. Shine ya dawo,yana tsugunne saman qafafunsa da cups guda biyu masu cike da zamzam mai sanyi. Batayi musu ba ta miqa masa hannun,yatsunsu suka hadu da juna,sai ya zare hannunsa a hankali. Kauda kanta tayi tana juya yadda zata sha ruwa a gabansa,yana zaune dab da ita,idanunsa ta tabbatar kuma suna cikin nasa. Kamar yasan me take tunani,kamar yasan abinda yake ranta,sai ya matsa gefe kadan yana zama sosai saman tiles din masallacin. A nutse ta shanye gaba daya,sai taji wata nutsuwa tana saukar mata a hankali. Ta sake satar kallonsa,baya komai don ya nuna kansa.....amma komai qoqari yake ya nuna wayeshi. A yanzun tana jin kawai kamar binne kansa yakeyi......tana jin wani binnnan mutum ne kawai suke rayuwa dashi,ba ainihin haqiqanin sheikh haisam na agadez ba. *zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 08187255862 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 08187255862 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 27* Ba a nan kawai ba.....sanda suke takawa a hankali ita dashi,tana daga gefansa.....iskar dare me tarin nutsuwa da wani irin sanyi tana kadasu. Kusan dukka inda sukebi kamar abun shiri,ma'aurata ne guri guri cikin yanayi na soyayya da zai dauki hankalin duk wanda ya gansu. Wasu a kwance daya yayi pillow da cinyar daya......wasu a zaune suna hira......wasu karatun qur'ani.....wasu kuma dukkansu bacci suke kusa da kusa da juna,yayin da wasunsu kuma suke maqale da hannun juna suna tafiya zuwa gurarensu. Idanunta yawo kawai yakeyi a kansu,haka kawai takejin komai yana burgeta,haka kawai takejin yanayin duk da take kalla yana burgeta. Ba soyayya sam cikin tsarinta.....saboda ba kalan namijin da takejin yakai ya mallaketa......amma a yanzun batasan me yasa couples din suke burgeta ba. Qarar da yaji wayarsa tayi ta Bluetooth din dake kunnensa shi ya sanyashi cirota daga qaramin wallet din hannunsa. Beeno ne ya ajiye masa saqo,wanda ya tsara saqo kawai dama banda kira har sai sun kammala umara. _muhammad ya damu.....yanason yaga 'yaruwarshi tunda ya rasa mamarsa_ shine kawai saqon. Wani nauyi yaji ya sauka a ransa,tausayin yaron ya kamashi,sai ya maidawa beeno din amsa a taqaice. _ka bashi haquri,zasu hadu a Ethiopia_ Daga can wani sashe na daban take kallonsu,yana kwance saman cinyarta da alqur'ani a hannunsa,ita kuma ta tura yatsunta cikin sumarsa tana hargitsata a hankali tana kuma biye da sautin karatun nasa. Sautinsa ne sama da natan,amma dukka sound dinsu ya cakude ya bada wani launin qira'a me dadi. Batasan me ya saukar da murmushi saman fuskarta ba......sannan ya fusgi hankalinta zuwa ga kallonsa don taga ko shima ya gani?. Still idonsa nakan waya,wani abu taji mara dadi ya tsaye mata,saita janye dubanta a kansa ta maida kansu,daidai sanda shi kuma ya juya a hankali yana dubanta da wani yanayi da zai wahala ka gane ita yake kalla. Karon farko ya zuba mata ido da wani kallo na daban.....tausayinta a karon farko ya soma ratsa zuciyarsa da qarfin gaske. Yaji zuciyarsa tana nauyi,yana rayawa a ransa,idan shine ya rasa nanay dinsa yaya zaiyi?. Inda ya rayu ba noorah......ba hussam.....ba rumaisa.....ba khansaa.....ba Aareef yaya rayuwa zata kasance masa?. Tausayinta yakeji da gasken gaske.....dukka batasan dadin wadannan ba?. Batasan dadin uwa ba.....batasan dadin 'yan uwa ba. Ta rasa da yawa cikin rayuwarta ba tare data sani ba.....ta rasa wasu bangarori masu matuqar Muhimmanci bata gane ba. An kange mata rayuwa an tsaidata a wani muhalli guda daya,ta dauka iya haka ta morewa rayuwarta. A yadda ta motsa ya fuskanci dauke idanu tayi daga kallon wani abu,kallon wani abu da ya tabbatar shine. Yaji a jikinsa a dazun,amma kuma yanason kamata a yansu da kansa......yanason kamata yadda ba zata iya musa masa ba,don haka yayi kaman ya dauke kai.....yayi kaman ba yaci gaba da abinda yake gabansa ne. Karo na biyu ta sake waigowa,tana jin wannan haushin can qasan ranta. Me yasa yakeson maidata mayyar kallonsa?,me yake dashi me janye hankali har haka?. Ba haka take ba.....ta sani ba haka dabi'arta take ba. Komai kyau....komai isar d'a namiji baya da wannan muhimmancin a gareta.....me yake shirin canzata?. Da wani irin zafin nama ya waiwayo,ya kuma kamata kaman yadda yayi timing. Ta dan razana don haka tayi saurin kauda kanta. Murmushi ya saki....wani kalan murmushi me sanyi. "Me yasa ba zaki bar wuyanki ya huta ba akhnan?" Har tsakiyar tafin qafarta taji yadda ya kira sunanta. Wani irin accent yayi amfani dashi daya sanya sunan ya sauya kamar ba sunanta ba....kamar ba sunan data saba ji daga bakunan mutane ba. Izzarta ta motsa kadan,saita hade ranta sosai,tana ji a ranta bai kamata haka taci gaba da kasancewa ba,bai kamata ya ganta tana kallonsa ba har haka. "Da akayi me?". Wannan karon murmushin nasa sai daya bada sauti kadan,murmushin daya masa kyau ainun,har ya dauki hankalin wasu 'yammata dake zaune daf da inda zasu wuce,kuma akan idanunta,tana ganin yadda dayar ta tabo 'yar uwarta a dabarance,tabar danna wayar da takeyi ta xuba masa idanu kuwa. Idanunta ta dauke a kansu tana jin wani abu ya matse a qirjinta. "Me yasa duka wannan?" Ta tambayi kanta,me yasa takejin kanta kamar ba ita ba?,kamar ba ita akhnan ba?,me yasa?. Ya shirya shayar da ita mamaki,don haka ya miqa yatsunsa ya kama habarta ya juyo da fuskarta zuwa saitin tasa cikin ba zata. Tazarar dake tsakaninsu ya hade yana duban tsakiyar qwayar idanunta,a hankali ya motsa labbansa,tafiyar tasu dukka su biyun tana komawa very slow kamar wadanda qafafunsu sukayi sanyi. "I'm your halal.....ki kalleni kai tsaye kaman zaifi your highness.....kina yawan kauda kai,kaman bakisan kina kallona bane" Kasa cire idanunta tayi daga nasa,kaman yadda shima ya zabi ci gaba da karantarta ta cikin qwayar idanunta masu kalan blue da haske qwayayen haram ke sake haske masa su. Wani unique qwayan idanu da suka banbanta da irin wanda kowa yake dashi. "Sun narke dukkansu......amma inda zakace wani abu yanzu kowannensu saiya qaryataka" Maleek dake tsaye daga nesa kadan dasu ya fada yana riqe da falaak sosai cikin jikinsa kamar wani zai qwace masa ita,saidai kuma akhnan da haisam din dukkansu sun dauki hankulansu fiye da yanayin da suke ciki. Duk da yanayin kunyar da maleek keta saka falaak adan tsukin......amma a yanzu....a daidai lokacin saita hango wani boyayyen abu....wani boyayyen abu da yafi qarfin kansu ita da maleek din gaba daya. Wani abu da yasa taji kamar zata narke.....kamar bata taba ganin abun burgewa a rayuwarta ba irin tsaiwar akhnan da haisam a gurin......duk da basajin maganan me suke.....amma ko daga nesa duk wanda zai wuce sai ya kallesu,sai kuma ya sake waiwayowa ya sake kallonsu,saboda wani irin perfect match da aka tasa a gurin. A hankali ya sake mata habarta,taja baya da sauri tana sunkuyar da kanta qasa. Me yasa ta tsaya?,me yasa taci gaba da kallonsa?. "Yaaa akhnan" Muyar falaak ta fusgi kunnuwanta,falaak din data kasa jurewa sai data kira akhnan din,duk da yadda maleek yaso ta bari su mamayesu kawai. Tunda yaji muyar falaak ya tabbatar tare suke da maleek. Sauke hannuwansa yayi ya soma laluben nata hannayen cikin nasa ba tare daya waiwaya ya kalli inda suke ba. Sosai ya matsesu cikin nata,dumin dake jikin tafin hannun kowannensu yana zagayawa sassan jikin kowannensu. Idan yace bayason tafukan hannayen ta yayi qarya......idan yace dumin da yakeji a ciki basa burgeshi yayi qarya......idan yace siraran dogayen yatsansa da suke shigewa cikin nasa basa burgeshi yayi qaerya. Karon farko a rayuwarsa daya tsaya karantar yanayin hannun wata diya mace.....kaman yadda ta zama mutum ta farko daya fara saka hannuwanta cikin nasa irin haka. (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) "Banaso ki kalli kowa......shi yasa nace ni ki kalleni kai tsaye a duk sanda hakan yayi miki" Ya qarashe maganan yana duban idanunta,can qasan ransa kuma yana jin kamar maganar tayi nauyi.....kaman bai furta maganan daidai ba. "Maleek na tahoha......boundaries please" Ya fada muryarsa can qasa kamar wanda kejin bacci,abinda ya tayar da duk wata tsiga kenan ta jikinta,saboda sai daya kawo bakinsa saitin kunnenta sannna ya qarashe maganan. Ta rasa wannan boundaries da yake saka mata na meye......ta rasa me yasa yake yawan nanata mata kalmar a duk sanda zasuyi wata hulda data hada da maza a gurin. Sakin hannunta qwaya daya yayi,sannan ya maidata a gefan kafadarsa daya suka fara takawa a hankali suna tunkarar su maleek dake tsaye a gurbinsu. Idanunsa akan fuskar maleek kawai suka tsaya,yana kallon yadda maleek din ya sunkuya a hankali yayi magana da falaak. Bai kalleta ba.....amma in blurry vision yake ganin kamar ta saka tafin hannunta ta lullube fuskarta. Baisan me yace da ita ba.....amma yayi imanin gulmarsu sukayi. Sakin hannunta yayi a hankali ya miqawa maleek sukayi musabaha,yana jin falaak na gaidashi. "Barka da warhaka Aman-nin" "Barkanki kina lafiya?" "Alhamdulillah". "Aman-nin......me kenan habibty?" Duka sai falaak din taji ya aza mata nauyi. Tun daga saukarsu zuwa yanzu a yau din ita kadai tasan nauyin da maleek yake sakawa takeji. "Yaren Tuareg ne.....yana nufin yaaya" "Zaa koyamin?" Ya tambayeta yana narke murya idanunsa dukka a kanta kamar ya cinyeta. Kai ta daga a hankali. "Kun kammala umrar?". Haisam ya katse tattaunawar tasu,saboda lura da yadda maleek yake neman sauka daga layi. Maido dubansa maleek yayi ga haisam din,dama kuma abinda yakeso kenan,sai haisam din ya watsa masa harara. Dariyarsa ya danne,ya sani muddin idanun haisam suna kanka baka isa kayi abun arziqi ba. "Habibty ta gaji......gobe zamu qarasa sa'ayi" Kafada haisam ya daga dukka biyun. Kallon akhnan falaak tayi,wannan qaunar.....wannan 'yan uwantakar,sai taji ta kasa jurewa duk da dariyar da take boyewa. Ta taka da sauri yana rungume akhnan din don ta sani ba lallai ta fara samun hakan daga akhnan din ba. "Yaa biftu.....Essaghlegh-kem(nayi kewarki).Temegded temhust(kinyi kyau)". A karon farko taji wani 'yan uwantaka na ainihi yana ratsata sanda falaak ta rungumeta,sai ta samu kanta itama da zagaya hannu ta rungume falaak din cikin jikinta,sannan ta amsa mata itama cikin yaren Tuareg din,don suna ganin shine kadai safest yare da zasuyi maganansu cikin sirri. "Kice wani abu daban mana falaak?,ta ina kikayi kewata?,ina kuka bace?". Baya kadan falaak taja tana dariya a kunyace,amma kafin tace komai taga haisam din riqe da hannun maleek suka qara taku kadan gaba dasu suka basu tazara. " Ya biftu......man dinki....man dinki shine ya koremu,yace bazai hada masauki da habeeb ba.....ina jins......" "Habeeb?" Akhnan ta samu kanta da maimaitawa tana zubawa falaak ido. Kunya ta saukarwa falaak,tasa tafin hannunta tana toshe bakinta gami da sakin dariya. "Afwan ya biftu......amma shine ya koremu seriously fa........basan wanne irin hot love zaa baza ba haka da ba'a gayyatarmu" Ta qarasa fada qasa qasa tana raba idanu. Fuska akhnan din tadan hade tana hararan falaak "Baki da kunya sosai ashe falaak ?.kin manta?Nekk a weltma-kem tameqqart.(ni yayarki ce?" Ta fada tana komawa ainihin akhnan dinta. Murmushi ta sake saki a kunyace,sai suka taka suna zama saman tiles din gurin. Idanu kawai akhnan ta zubawa falaak,yadda take magana yake bata mamaki. Me maleek ya bata haka kaman ta zauce a kanshi?. "Ya isa" Akhnan ta fada a hankali tana dagawa falaak hannu. Wani irin soyayya ne me zafi take gani a idanun falaak din,koda suna tare amma idanunta yana tare da maleek din,kamar yadda ta karanci kaman shike tsokanota daga inda yake. "Zamu wuce yaa biftu" Falaak ta fadi bayan ta miqe. "Byee" Akhnan ta fada tana daga mata yatsu,itama saita maida mata ta soma takawa tana nufar inda maleek din yake. Qasa ta danyi da kanta tana murza yatsunta. So take ta fayyace.....laifi falaak tayi?,ko kuma akan daidai take?. Wanne irin so ne wannan?,baiyi zurfi da yawa ba?. Tadan yi taku biyu baya don daidaita tsaiwarta,sai taji kaman ta dunguri wani abu,ta juya da sauri.....saurin daya bawa fuskarta daman shiga cikin nasa,sukayi musayar numfashi sannan tataka baya da sauri,saidai tuni ya saka hannunsa ya riqo qugunta. Da sauri ta daga ido ta kalleshi sanda take riqe cikin hannunsa,sai ya mata nuni da bayanta da idanu. Takalmi ne a gurin na mutane,wanda tabbas data taka koda bata fadi ba saita kusa faduwa,saita maida dubanta kansa,a hankali ya zame hannunsa yana sakinta amma still idanunsa cikin nata. Kallon nan yana mata nauyi da yawa,ko a yanzun sai taji idanunsa suna neman sanyata ta diririce,saita soma gyara zaman hijab dinta ko zata samu chance na lalubo nutsuwarta. "Coffee?" Ya motsa labbansa ya fadi a hankali idanunsa suna kan kwantaccen gashin gefan fuskarta daya fito. Manyan blue eyes dinta ta daga tadan kalleshi,haka kawai wannan karon yaji kamar an qarawa qwayar idanun nata haske,sai kuma ta zame a hankali ta motsa bakinta tana fadin. "Okay". *zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 08187255862 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 08187255862 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽 💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 28* A nutse take qarewa gurin kallo,shima ko ba'a gaya mata ba vip ne......ta sani vip ne gurin,don komai nasa a tsare yake. Hatta da butoci da cups da tray na tea din daban suke. Daya daga cikin ma'aikatan gurinne ya qaraso cikin girmamawa ya gaida haisam. Sai yayi magana dashi da yaren da bata fahimceshi ba. Juyawa yayi ba dadewa ya dawo da kalolin tea da coffee din ya ajiye musu ya juya. Kallonta yayi kadan sannan ya kalli tray din,ya dauki buta daya ya tsiyaya mata cikin madaidaicin cup din ya tura mata zuwa gabanta. "Akwai wani abu daban da kike da buqata?" Ya tambayeta yana kai nasa cup din bakinsa. Original oromo coffee......tea din daya jima dayin missing dinsa tun bayan shigarsa agadez. Kai ta girgiza a hankali,ta miqa hannu ta dauki cup din,amma kuma ta kasa kaiwa bakinta. Wani irin rashin sakewa da rashin sabo takeji,cin abinci a gabansa wani sabo kuma baqon abune a gurinta. Saita dinga juya cup din kawai cikin hannunta a hankali har sai daya lura da hakan. "Kina iya sha bayan ya huce?" Ya tambayeta yana sauke idanunsa daga kanta. Shuru ta danyi kafin a hankali ta dauki cup din takai bakinta. A yangance da nutsuwar izzarta tayi sipping sannan ta sauke cup din tana jin dadin coffee din yana ratsata. Idanunta ta maida cikin cup din tana kallon abinda yake ciki sosai abinda batayi ba a dazu,sai ta sake daga idonta tana dubansa. Girarsa ya daga mata dukka biyun yana aje cup dinsa. "Oromian coffee" Ya furta a taqaice,ta danbi lips dinsa da kallon wanda dumin coffee dinsa ya sake sanyawa yayi wani irin jaja jaja me kyau,saita dauke idonta a hakali zuciyarta na raya mata wani abu. Minti talatin kawai sukayi koma koma raffles don su sake hutawa sosai. Birra ta shigo har dakinta ta tayata rage kayan jikinta,tayi wanka ta fito ta sake shiryawa cikin kayan baccin guda daya data dauko mata. "Me yake damunki ne birra?....me kike sanda kika hadamin kaya ne?" Qasa tayi da kanta cikin Girmamawa "Tuba nake.....sheikh yace komai daya danganci gida a barshi a nan....umarnin dana karba kenan". Shuru akhnan din tayi tana kallon birra,tana kuma son gano dalilin daya sanyashi ya bada wannan umarnin. Bata gane komai ba,don haka kawai tace da ita. "Jeki" "Ki huta lafiya" Ta fada tana juyawa sannan ta fita. Duk da duhu daya mamaye dakin,amma hakan bai hana shigowar haske daga gurare daban daban na waje ba. Wani irin sukuni takeji a duk sanda ta bude lumsassun idanunta ta hangi hasken harami daga nan inda take kwance da kuma ginin ka'aba. "Astgafirullahal azeem" Ta samu kanta da maimaitawa tana tuna wannan kalmar.....wannan kalmar ita ta dinga ji haisam din yana yawan maimaitawa,wannan kalmar a yau batasan adadin sau nawa ta jita a bakinsa ba. Ta sake lumshe idanunta komai yana dawo mata sabo. Tun daga tasowarsu daga agadez,Niamey,jidda zuwa cikin haram. Dawafinsu da komai daya gudana a tsakaninsu yau din. Gyara kwanciyarta tayi zuwa rigingine tana zurfafa tunaninta. "Wayeshi......wannan rayuwar batayi kama da wanda aka yiwa alfarma ba" Ta motsa labbanta a hankali tana fadi. Tuna komai take in details,tuna yadda yake gudanar da komai da yanayin sabo na mu'amala da komai da komai ma. Akwai yanayi sosai daya bayyana sabo da rayuwa me tsada a tattare dashi.....akwai yanayi daya bayyana gogewa da iya mu'amala da mutane.....akwai yanayin da yake haska wani abu a tare da dukka motsinsa......yanayin dake bayyanawa idanu kaman ya saba hulda da manyan mutane. Ta yaya zai iya ganin manyan malaman harami haka idan har shi din ba wani bane?. Tambayar data sanyata miqewa sosai ta zauna tana rungume da pillow a qirjinta. Idanunta suna juyawa tsakanin dan haske da duhun dake gauraye a dakin. Wani irin shuru taji cikin kanta,ta juya qwayar idanunta tana jin sautin muryarsa yana dawowa cikin kunnenta. Ta lumshe idanun tana sake bibiyar kowanne sauti.... Kowacce magana da yayi mata a yau din. Yana da wata irin murya me taushi.... Mai sanyi sannan kuma me zurfin gaske da idan ya maka magana kakejin saukarta kai tsaye saman zuciyarka. Wata irin murya da idan ta jita koda da kalma daya take ne sai taji zuciyarta ta buga. A hankali ta sake lumshe idanunta tana wassafa fuskarsa cikin gizanniyar idanunta. Giant ne.....ta dade da lura da wannan....wani irin giant da tsaiwarsa kawai tana iya daukan hankalin diya mace,saboda murjajjen jikin da yake dashi,wanda ta dade tana kyautata zaton ma'abocin motsa jiki ne da daga qarfe daga yanayin structure din jikinsa duk da bata taba ganinta a sarari ba. Tana iya tunawa da dogayen hannayensa masu dogon yatsu da suka sha tareta daga shan kayi daga dawakinta. Wani irin dogayen yatsu da suke mata kama dana mutumin daya saba da iko. Motsinsa bame sauri bane......amma kuma yana da wani irin control da zafin nama idan yaso. Idanunsa sune mafi daukan hankali,manya ne ita kanta shaida ne akan wannan,amma ta lura wani lokacin daga shine?,ko halittarsu ce a haka?,sukan rage girma su lumshe sosai,har sai kayi zaton bacci yakeji,akwai wani irin calm intensity a tattare dasu me yawa. Sau tari idan ya kalleta,sai taji kaman yana ganin fiye da abinda ke saman fuskarta,har cikin jininta da jikinta tana jin yana da wani kebantaccen baiwa na iya karantar yanayin mutum ta cikin idanunsa,wannan yana daga cikin dalilin daya sanya take kaucewa dogon kallo daga gareshi. Eyebrows dinsa da suka kusa hadewa da juna......hancinsa daya zauna sosai saman fuskarsa.....shi ba siriri ba kuma shi bame fadi ba,ya hade duka siffofin guri guda. Ta lura dashi.....baya da yawan murmushi,amma aduk sanda yayin sai fuskarsa ta sauya da wani sirrin boyeyyen kyau da a iya lokacin murmushin kawai yake bayyana. Kawai komai nasa yana sake fadi da wani irin murya me nauyi da qarfi cewa he's not an ordinary man........amma me yasa ta gaza gane komai a kansa?,ta gaza gane ainihin wayeshi?. Lips dinsa data tuna saida dukka tsigar jikinta ta tashi,wani abu ya motsa mata sosai cikin jikinta wanda batasan dashi ba,saita samu kanta da curewa guri daya,ta matse pillow din cikin qirjinta sosai tana tuna yadda dumin hannunsa ke bibiyar kowacce jijiya ta jikinta da wani irin sauri ya sauke mata kasala da gajiya. (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) Wani irin mirginawa tayi tana girgiza kanta. "Why akhnan?.....me yasa?....me yasa?" Ta tambayi kanta tana girgiza kai. Ko sau daya a farke ko a sarari bata taba zama irin haka tana wassafa wani d'a namiji ba tunda take. Ba wani d'a namiji data taba zama tama tuna da cikakken sunansa bama nasabarsa ballanta siffofinsa. Ba wanda yayi wannan isar.....ba wanda matsayinsa yakai...me yasa saishi?. Wannan malamin?,wannan mutumin daya fara karya kusancinta da sultane,ya canja mata table na rayuwarta ya mallaketa da dukkan mugunta?. Ada idan ta tuna hakan ciwo takeji.....baqinsa take gani,amma a yanzun duk da zuciyarta ta maimaita mata sai taji bataji komai ba,bataji komai ba sai wani irin yanayi dake mamayarta.....bataji komai ba sai wani abu me kama da kewar idanunsa.....kewar muryarsa da wannan miskilancin nasa. Ta tabbatar a yanzun dare ya soma nisa,yadda kuma suka kwaso gajiya dole shima ya kwanta ya huta. Wani bushewa maqogoronta taji yayi,ruwa taji tana da buqatar sha,wani yanayi ya saukar mata da wata irin matsananciyar kasala a jikinta,saita zare pillow din,ta jawo jiki ta sauko daga saman gadon,ta saka hannunta tana tattare gashinta ta daure cikin scarf mahadin kayan baccin,sannan ta fara takawa zuwa living room din. A nutse ta bude qofan ta soma fitowa tana mamakin labulen fuskar ka'aba dake a bude,wannan yasa living room din baiyi duhu sosai ba,don haka bata buqaci kunna haske ko daya ba taci gaba da takawa tana duban sashen da yake tarwai da fitilun haram da basa dusashewa ko daukewa. Sai a sannan ta lura dashi,shine a zaune saman daddumar dake shimfide gaban gurin wadda ke dauke da tambarin hotel din. Cikin sujjada yake,wata doguwar sujjada da har ta dauko ruwan ta dawo tazo ta wuce bai dago ba. Haka ta dinga satar kallonsa har ta koma cikin dakin. Zama tayi gefan gadon,ta bude ruwan ta riqe a hannunta. Baya gajiya?,shikam baya gajiya ne?. Haka kawai takejin kamar ya mata wayo,tana nan zata kwanta tayi bacci amma shi ya gagara baccin. "To amma.....na gaji" Ta fada can qasan ranta. "Kisha ruwan ki kwanta,saiki tashi da wuri kafin asuba tayi" Zuciyarta ta bata shawara. Saidai koda tasha ruwan ta koma ta kwanta baccin kasa zuwa yayi. Tsintar kanta tayi da tashi a hankali,ta jawo qofar baya ta soma leqensa ta tsakanin space din. A yanzun a zaune yake,qur'ani ne kuma a hannunsa sautin karatunsa yana fita can qasa da wannan sautin nasa dake kusan narkar da zuciya. A hankali ta maida qofar ta rufe sanda yakai qarshen surar da yake karantawa,ta koma da baya a hankali har zuwa saman gadonta. Pillow ta sake riqewa sosai tana sauke ajiyar zuciya,kafin ta tashi a hankali ta bude jakarta. Littafinta na tarihi ta dauko,tarihin fiyayyen halitta,littafin data kammala na farko ta dauko wallafar ibn taimiyya,sai kawai ta kunna fitilar gefan gadonta ta matsa rub da ciki ta bude ta dora karatu. Batasan adadin awannin data kwashe ba a zaune,don ko bacci cikakke bata ji,tasan dai ta fada wata duniya daban da wadda take ciki. Zata iya cewa karatun a yau ya mata amfani fiye da kullum,saboda gata a gurin,gata a kusa da inda komai ya wakana na tarihin rayuwarsa. Taga abubuwa masu yawa,taga gurare masu muhimmanci gurin amsa addu'a,ta sake fahimtar abinda ya sanya haisam din bai yarda ya kwanta yayi cikakken barci ba. Sai taji gaba daya ta sake daura tata damarar,sai taji kaman duk zuwan da takeyi umra a baya kaman wasa ne,wannan zuwan.....wannan lokacin shine sahihin lokacin zuwa na gasken gaske. *_W A S H E G A R I_* Duka washegarin basu hadu dashi ba,tun daga asuba har zuwa dare,don ita dimma washegarin saita zamar mata kamar an mata allura an kuma sake qara mata qaimi akan ibada. Sam bata huta ba,kusan yini tayi cikin haram tana addu'o'i. Har addu'ar da bata dauka cewa zata iya ba. Addu'o'in da bata taba kawowa a ranta wataran zata roqa ba. Shi take kalla a sanda yake zaune yake kuma dadewa saman abun sallah hannuwansa a sama. Wannan ya mata tasiri qwarai,ya kuma cire mata qyuya da ganda na dogon zama tana addu'a. Tayi zaman addu'ar da tunda take a rayuwarta bata taba irinsa ba. A hankali sai takejin wani tarin nutsuwa suna shigarta. Bayan sallar la'asar ne birra ta iskota,tana zaune a lokacin tana hutawa kawai bayan ta shanye ruwan zam zam cup har biyu. "Yallabai yace.....bayan sallar isha'i zaku qarasa sa'ayinku" Kadan ta daga kai ta kalleta,kaman ta tambayeta inda ta ganshi sai kuma ta fasa ta daga mata kai kawai. Sai datayi sallar isha'i sannan ta wuce masaukinsu. Ta buda qofar ta tura,ba alamun akwai mutum cikin suit din nasu. *zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 08187255862 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 08187255862 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 29* "Ki shiryamin komai ki wuce,zan qarasa shiryawa da kaina" Tace da birra tana zare qaramin hijab din data dora saman abayar jikinta. Karon farko da tayi ta'ammali da hijab har haka a rayuwarta,wadannan hijabs dinma data gani cikin kayanta batasan waye ya dinkosu ba. Haka kawai taji a yau din tanason shiryawa da kanta,kaman bai dace ba kuma birra ta wanzu a suit din nasu ba. "Wai fa...." Ta fada tana duban birra dake shirin wucewa ciki. "Hijabs dinnan fa?" Qasa birra ta danyi da kanta tana sake boyayyen murmushi. "Ba iya su kadai ba.....duka kayan cikin luggage din......dama wanda na shigo miki dasu dazu,sheikh muhammad ne...." "Ya isa" Akhnan ta fadi a nutse tana miqewa,sai birran bata sake cewa komai ba ta wuce ciki itama ta bita. A baya bata damu da tsaiwa duba komai ba,amma a yanzun bayan ta fito a wankan saita samu kanta da bin komai da kallo. Abayas din....hijabs.....bathsetdinta......set na mayukanta dama komai......ba asalin komai nata bane. Komai ya canza da wani irin tsari. Juya su take tana sake kallo,komai cikin wani tsari yake da burgewa,kaman yadda komai din yake nuna asalin tsadarsa. Iska ta fesar a hankali,ta lura da banbance babancen,tayita mamaki ita kanta a karan kanta,amma ta dauka shirin birra ne,saidai ko data raya hakan a ranta ta danyi kokwanto,yaushe birra tasan abubuwa masu tsada irin haka?. Yau cikin shigar fari ta shirya kanta. Farar baya ce me wani irin duwatsu masu sheqi da walqiya ruwan silver dake cancanza kaloli da duk abinda yayi reflecting nasu. Silver ash din snickers ta saka,sannan ta rufe kanta da Malaysian hijab shima daya kasance color din. Ita kanta data kalli kanta da kanta a madubi saida ta lumshe idanu,murmushi ya qwace mata,wani irin murmushi me sanyi. Bata taba sanin irin wannan shigar zata mata kyau ba sai yanxu,bata taba sanin zata zama daya daga cikin suturu da zasu dace da jikinta ba sai yanzu. Taja da baya tana duba lokaci,saita yanke ta fita ta living room din ta samu koda lemo ne tasha kafin su wuce. Waya ce maqale a kunnensa saboda barin Bluetooth dinsa da yayi a daki,fitowarsa kenan daga wanka khansaaa ta kirashi. Ya daga wayar amma qishirwar da yakeji ta tilasta masa fitowa neman ruwa sannan ya koma ciki ya shirya. Daure yake da farin towel,fari qal dashi me matuqar laushi. Daga qugunsa ya daureshi sosai,ya kuma tsaya masa iya qasan gwiwoyinsa. Faffadan qirjinsa.......dogaye kuma tsayyayun qafafunsa.......yalwatacciyar kafadarsa......lallausar gargasar dake kwance saman qirjinsa dama duka sassan jikinsa sun bayyana suna zamewa fatarsa me cike da sulbi da wani haske na musamman ado. Shafaffen cikinsa ya taimaka wajen bayyanar qirjinsa dake cike da muscle,da wasu muscles din dake lullube da fatar saman shafaffen cikinsa. Bai kula da ita ba kaman yadda bata kula dashi ba,don ba magana yakeyi ba yana dai sauraren khansaaa ne kawai kaman yadda al'adarsa take sauraro kafin yayi nasa bayanin,yana kammala zuba ruwan ya soma rufe gorar ruwan,daidai sannan ta daga idanunta daga latsa wayarta da takeyi cike da mitar ba wanda ya kirata tun daga jiyan zuwa yau?. Koda sultane kuwa?,koda aisa?,koda shehnaz?. A hankali ta daga idanunta don ganin inda zata zauna,saidai maimakon ganin gurin zama sai idanunta sukayi wannan kyakkyawan ganin,daidai sanda shima ya aza idanunsa cikin nata. Hannayenta ne suka dauki rawa,ta furta. "Subhanallah" Da dan raunin murya muryartata tana shaking,sannan ta juya da sauri tana bashi baya,juyawar data sanya wayar hannunta sulalewa ta fadi a qasa. Idanu ya zuba mata ta baya yana karantar yadda ta rude duka lokaci guda. "Zan kiraki.....minti daya" Yace da khansaaa,sai ya zare wayar daga kunnensa ya kashe ya ajiye saman dan table din dake kusa dashi. A nutse ya taka zuwa saman daya daga cikin kujerun,ya dauki bathrobe din dake ajiye gefanta ya zura ya kama igiyoyin ya daure ba tare da yace da ita komai ba. Wata irin kunya cakude da wani nau'in tsoro ne suke dabaibayeta. Wani yanayin buguwa zuciyarta keyi tamkar wadda tayi tseren gudu na kilometers masu yawan gaske. "Banyi tsammamin zaki fito ba" Ya furta a hankali don ya bata relief daga yanayin daya lura ta shiga,don har yanzu jikinta rawa yake idan ka lura sosai. "N....nima b....ban sani ba" Ta amsa mata muryarta na rarrabewa saboda bugun da zuciyarta takeyi. Taku kadan yayi ya isa bayanta don ya dauki daya towel din dake gefanta saboda tsane damshin sumarsa. "Kina iya juyowa". Dab da ita ta jishi,dab da itan da takejin ko yaya ta juyo tabbas cikin jikinsa zata fada,saita kasa motsawa,qamshin shower gel dinsa yana buso mata a hankali,saita lumshe idanunta tana jin zuciyarta kamar tana shirin rikitowa daga qirjinta. Ya dauki towel din a nutse ya taka yana matsawa daga gurin. Wayarsa ya koma ya dauka sannan ya nufi qofar dakinsa yana shirin sake kiran khansaaa. Ajiyar numfashi ta dinga saukewa a jejjere,ta saka tafin hannunta tana dafe qirjinta a hankali,sannan taja jikinta ta zauna saman kujerar. "Wai Allah na..." Ta fada tana zare idanu,sai kuma murmushi ya qwace mata,kafin kuma a hankali idanunta ya sake dauko mata hoton yadda ta ganshi. "lean, well-built body" Ta furta a hankali,sai kuma ta kama bakinta tana rarraba idanu. "Me ya kaiki?,ina ruwan ki da jikinsa?,idan ya jiki kuma fa?" "Baiji ba bazai kuma ji ba in sha Allah" Ta fada tana qoqarin ture tunanin ta hanyar kiran shehnaz,saidai kuma hoton ya kasa barin idanunta. (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) "Haka jikinsa yake?" Taci gaba da fada cikin ranta. Favorite qirar da tasha kwatanta son samu jikin namiji,saidai abinda ya fara sare mata shine.....yawan mazan da muke dasu a qasashenmu basu maida motsa jiki a bakin komai ba. Kusan dukkaninsu qirar jikinsu irin na matansu ne.....damtsen miji da mata duka baka banbancewa kusan iri daya ne. A nata tsarin.....a nata ra'ayin komai na mijin da takeso ya zamana yasha banban dana mace.....asalin qira da siffar jarumta sosai,jarumi takeso....zakin gaske.....amma kuma" Saita dakata da tunanin a ranta kadan. "Akwai wasu siffofi kaman....." Nanma ta katse tunanin kamar me tsoron tattaunawar yau da zuciyartata ma. Jin muryar sultane ya yanke kowanne tunani daga ranta. Cikin doki kewa da qauna ta soma gaidashi. Daga nasa bangaren ya fita farinciki da jinta. "Komai lafiya ko?,duk da muhammad ya tabbatar min" Kai ta daga tana murmushi. "Lafiya alhmdlh....bappi ka manta dani,baka nemeni ba" murmushi yadan saka me sauti kadan. "Inde muhammad ya kirani muka gama waya lafiya dashi,to na tabbatar kema lafiya kike". "Amma bappi....kana lafiya?,muryarka si faible(so weak)" Murmushi ya sakeyi,tabbas idan yaje yana jinsa lafiya lau a kwanakin to yayi qarya,amma kuma ba buqatar ya gaya mata hakan. Nutsuwarsu da sake gamsuwa da zama da junansu yafi buqata a yanzu,ba wani buri da yake dashi sama da wannan a yanzu. "Lafiya qalau nake,ina hutawa ne kawai" Kai ta daga a hankali. Hira kadan sukayi ahmad almaz ya karba. Taji dadin magana dashi sosai,yayi magana da ita kaman yadda yaya zaiyi da qanwarsa,wani feeling wani yanayi data rasa a yanzun data sameshi sai takejin kamar ta fara zama completed. Daga nan shehnaz ta kira,tana kira din kuwa ta daga kamar zaman jiranta takeyi. "Ina da niyyar nemanki kenan kiranki ya riga nawa shigowa". "Me ya faru?" Tambayi shehnaz din daidai sanda qofar dakinsa ta bude ya fito. Da sauri ta yiwa kanta linzami ta hanyar zare idanunta daga inda yake takowa. Ta yiwa kanta alqawari ba za'a sake maimaita abun jiya ba duk yadda zaikai gayi mata kyau,saita tattara hankalinta akan shehnaz. "Kwana aisa tayi tana kuka.....ta iso cikin wani yanayi daya daga hankalina. Sahel couture ya samu matsala biftu......dole ne na gaya miki wannan saboda kina gurin da ake amsar kowacce addu'a ta alkhairi. Anyi asarar maquden kudaden da idan ba wani ikon Allahn ba sahel ya tsaya da aiki har abada......tace batasan ya akayi ba,amma dukka kudaden sun fita dasa hannunta ne da sahalewarta,batasan kuma ya akayi haka ta faru ba......mammina ta yanke hukunci.......ta dakatar da aisa.......ta kuma ce zata kafa committee na bincike a kanta......kuma zata fuskanci duk hukuncin da aka tanada akan wanda irin haka ta faru ta sanadinsa". Wani irin sanyi hannu da qafafuwan akhnan sukayi.....wani irin yanayi da ta gaza tantance ame take?. Aisa kuma?......aisa dai?. To me zatace?,me zatayi?. Sahel couture din daya zama alfaharin sultane?,sahel couture din data dauki alqawarin saita kaishi matakin da sultane sai yayi alfahari da mallaka mata shi din da yayi?,to me yake faruwa haka?. A hankali taji an zare wayar daga hannunta,don dama a handfree take amma da lower volume bame qarfi ba. Daga idanunta tayi a hankali sai ta bishi da kallo,yana tsaye a gabanta,ya kuma sanya wayar a kunnensa. Tana jin sallamarsa da yadda shehnaz ta amsa da sauri ta fara gaidashi. "Ki sanar da aisa.....ni nace ta koma Niamey yau.....ta bude office taci gaba da aiki,duk wanda ya tambayi dalili kome yasa......kice ta fada masa CEO tace ta koma......ki fada mata.....zan nemeta qasa da awa shirin da hudu zamu tattauna" Daga akhnan din har shehnaz mamaki ne ya kamasu. Shehnaz dai ta sani......ba wanda keda qarfin ikon tada hukuncin mammina duk fadin niger ma ballantana agardez......agadez dinma cikin masarautar da kowa ya sani tana da cikakken iko a kanta?. Ta dauka zai miqa mata wayarta ne......amma maimakon haka sai taga ya kasheta ya jefata cikin aljihunsa. "Muje" Ya fada da wata nutsuwa yana dubanta,sai ta miqe tsam ta soma takawa tana wucewa ta gabansa zuwa waje. Duk da zuciyarta a nauyaye take sosai da tarin tunane tunane,amma hakan bai hanata ganin idanuwan mata sosai akan haisam din ba. Jifa jifa idanunta suna gane mata,saidai abinda bata sani ba shima yana gani?,ko ita kadai take gani?. Still idanunta basu gaza gane mata wannan soyayyar ba.....wannan soyayyar da kake iya ganinta ko ina a sararin masallacin dama gurare daban daban. Ma'aurata cikin shauqin soyayya,wasu da yara wasu babu sai iya su kadai. Wannan yanayin ya dinga debe mata kewa yana ware mata zuciyarta a hankali,musamman da taji lallausan sautin nan nasa yana fadin. "Allahu akhbar.....Allahu akhbar....subhanallahi wabihamdih......subhanallahil azeem" A sanda suke tattakawa saboda gabatar da sa'ayinsu. Akan safa suka tsaya kaman yadda tsarin yake,suka fuskanci ka'aba ita dashi. Sukayi dukkan kabarbari da addu'o'in da akeyi sannan suka soma nasu personal. Ta kammala nata addu'o'in amma tsaiwarsa da irin nutsuwa da take hanga a tattare dashi ya zama wani abu daban.......dukka tsarinta na hanawa kanta satar kallonsa a wannan lokacin ya wargaje. Wani irin kushu'i take hanga da zallar qanqan dakai gaban ubangiji,yanayin daya qara mata qaimi,takejin kamar akwai tarin addu'o'in daya kamata tayi batayisu ba.....kaman tana da sauran buqatu daya kamata ta roqa,kawai sai taji zuciyarta tana narkewa sosai a gurin. Sake maimaita addu'o'inta take,sai taji wasu suna shiga cikin kanta suna kutsowa ta bakinta. Aisa lamarin sahel duk sai taji kaman ya kamata takai lamarin gaban sarkin sarakuna. Ko meye ya kasance da sauqi.....sahel couture nada matuqar muhimmanci a gurinta.....kamar yadda aisa keda nata tarin muhimmancin. Da wani irin taushi ya sauke hannuwansa,maimakin ya barsu a qasa a hankali kamar jiya.....da wani sanyi taji ya kusa tafin hannunsa tsakiyar nata. Ta sauke wata irin ajiyar zuciya tana jin nutsuwa na saukar mata. Wani irin yanayi da ta kanji a duk sanda ya riqe hannunta ya fara bin jikinta,suka fara takawa suna gangarawa zuwa marwa da tarin addu'o'i da cikakken koyi da yadda ibadar take. *zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 08187255862 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 08187255862 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 30* A yau da suke sa'ayi tsakanin safa da marwa din,wani mutum take gani na daban......wani muhammad haisam take gani ba wanda take gani ba. Wata siffa tasa....other side nashi da bataga komai ba a baya sai yanzu. Batasan adadin sau nawa ta saci kallonsa ba,a sanda ta lura zuciyarsa tayi wani irin zurfi da nisa gurin ibada. Hatta da kamanninsa a yau sai take ganin na dabanne. Bai bata qafarsa ta taka kama jiya ba......amma yau dinma hannuwasa suna zagaye da kafadunta dako ta ina. Ko sau daya bai bari wani d'a namiji ya gogi kafadarta ba.....ko sau daya bai bari ta shiga inda za'a matseta ba. Wani double peace takeji.....wata irin nutsuwa.....wani kusanci......kusancin daya sanyata ta bishi da kallo a sanda sukazo daidai green light,inda maza ya wajaba suyi tafiya da sassarfa. Ya soma zame hannunsa cikin nata......ya soma takawa da sassarfa da wani irin energy kamar jarumin da zai shiga fagen yaqi tsakiyar abokan adawa. Mazane daruruwa ke tafiya cikin sassarfa a gurin,amma sai nata idanun suka tsinceshi shi kadai a cikinsu. Ya qetare maza da yawa,amma duk wanda ya gifta sai taga banbanci me yawa tsakaninsa dashi. Tsaho cikar jiki da murjewa dama yanayin kuzari. A duk sanda ya wuce da sassarfa kafin su sake hadewa sai taji wani irin loneliness ya sauka a hankali ya lullubeta. A duk sanda ya zame hannunsa daga nata sai taji kamar ta koma wani empty.....kamar ita daya tayi saura a duniya. "Subhanallah" Ta fada tana sauke idanunta qasa a hankali tana qoqarin maida kanta ga ibada. Wata irin ibada tayi da iyakacin imaninta bata taba irinta ba duk zuwanta gurin. Daren ranar gaba dayansa cikin harami suka qarar dashi,ya mata tayin tafiya masauki amma sam sai taji tafi qaunar zama a nan din. Har kashi uku yana cewa ta tafi,amma bata tafin ba sai bayan an idar da sallar asuba,bacci ya soma fusgarta da gasken gaske sannan ta wuce zuwa masaukin ba tare data nema inda yake ba. Doguwar rigar bacci kawai ta sauya ta zube saman gadonta,bata dauki dogon lokaci ba kuwa bacci yayi awon gaba da ita. Baccin da knocking din da taji ana mata shine ya tasheta. Da qyar ta bude idanunta tana jin kanta ya mata nauyi. Ta buda bakinta don tambayar waye ma taji ba zata iya ba,don tana kyautata zaton birra ce,don haka kanta tsaye kawai ba tare da tunanin komai ba ta sauka qasa sa hargitsatsen gashinta da rigar baccin data lafe mata a jikinta da ko brazier babu ta doshi qofar. A kasalance ta bude qofar tana murza idanunta tana shirin fara yiwa birra qorafi. Narkakkun idanuwansa ya zube saman fuskarta a farko....fuskar da tayi wani yanayi daya qara mata kyau saboda qananun gashin gaban goshinta zuwa kunnuwanta da suka kwanta sosai suka qawata baby face dinta. Uwa uba kuma gashin kanta daya hargitse yana rufe wani sashe na fuskarta wanda taketa qoqarin janyeshi kada ya shigar mata baki,bakin da taketa qoqarin son budeshi tayi masifar daya lura ta iya ta musamman akan birra idan ta mata ba daidai ba. Ba tare daya shirya ba.....cikin wani irin yanayi idanunsa suka zarce a hankali suna sauka saman qirjinta. Kallon daya zama guda daya tak amma me wani irin qarfin da yaji kamar an saka wani abu me matuqar qarfin magnet an zuqi kowanne jini dake zagaye da jijiyoyinsa.....kamar an mannashi da wata na'ura dake bada sinadarin shocking dake iya girgiza kowacce gaba ta jikin dan adam. Suna tsaye kyam tamkar an haliccesu ne saboda su tsaya a gabansa a wannan rana. Sun bayyana kansu tun daga shape dinsu da yadda suka tsaya cas a qirjinta kaman an daidaitasu. Komai na siffa da kamanninsu sun fito.....abinda kawai ya zama hijabi a tsakaninsa dasu shine yaloluwar rigar baccin data manne jikin fatarsu. Sai da ta samu nasarar maida gashin nata kafadar hagunta yabi dogo fari tas din wuyanta sannan ta daga idanunta taga kuma waye tsaye a gabanta. Wata iri mahaukaciyar razana tayi,taja baya da sauri da siraran qafafunta dake rawa,ta saka hannu da nufin maida murfin qofar ta rufe. Saidai kuma hannu daya kawai ya saka ya tokare qofar ta gaza rufeta. Da hannu daya ya dakatar da motsin qofar,sannan a wahalce cikin wani yanayi me wahala ya daga wayarsa yana miqa mata,yana kallon qwayar idanunta da idanunsa da suka canza kala cikin qasa da minti daya,don bazai kuma gangancin kallon qirjinta ba duk da ta saka hannayenta dukka biyun ta cukuikuye gaban rigar. "Magana akeson yi dake" Ya fada muryarsa tana harhadewa. Hannu daya ta saka ta karbi wayar kamar walqiya sannan ta koma bayan qofar tana qoqqarin turata. Ta turata din kuwa ta rufeta bam alamun yabar bakin qofar kenan. Ta jima tana maida numfashi,hannayenta dukka suna kakkarwa kamar wadda aka yiwa wanka da ruwan qanqara cikin tsakanin hunturun sanyi. Wani dogon numfashi ta aikewa hunhunta sannan ta fesar a waje,abinda ya dawo mata da wani sashe kadan na nutsuwarta. Wanne tsautsayi ne ya kaita rayawa birra ce tayi mata knocking?,wanne tsautsayi ne ya kaita buda qofa a haka?,abinda sam ba halinta bane?. Tunaninta ya katse sanda wayar ta dauki wani daddadan sauti,ta maida dubanta kan wayar da bata gane wacce irin waya bace ballantana kamfanin data fito. Abu daya ta iya ganewa inda zata daga kiran,saita daga din kai tsaye saidai da dan mamaki tattare da ita ganin sunan maleek ne akai. "Tantiii...." Taji muryar falaak can qasa kamar sautinta baya fita. Gaban akhnan yadam fadi,saboda yanayi ne da bata taba jinsa tattare da falaak ba. "Tanti......don Allah kizo......mutuwa zanyi wallahi.....maleek ya kasheni". Sai kuka ya ballewa falaak din. Dukkanin ilahirin jikin akhnan ne ya dauki rawa,wani irin tashin hankali ya rufto mata. "Falaak" Ta kira sunanta da wani irin tsoro da kuma nauyi a muryarta. "Kisa falaak?.....kina ina?". "Haisam zai kawoki" Taji muryar maleek a raunane maimakon ta falaak da suke magana. Abinda ya sake rudata kenan,duk jikinta ya sake daukan rawa,batasan sanda ta bude qofar da hannunta ba cikin sassarfa ta nufi dakin haisam din ba tare data tuna yanayin rigar dake jikinta ba,tana jin zuciyarta kamar zata ballo qirjinta ta fado,tsoro da tashin hankali suna mamayeta. (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) Bai taba jin yanayi irin na yau ba tunda yake a rayuwarsa dangane da mace. Bai taba tsintar kansa a mawuyacin yanayin da yakeji a yanzu cikin jikinsa ba game da d'iya mace. Ya sani basai an gaya masa ba,tun daga farkon balagarsa ya fahimci irin nau'in halittarsa,tun daga sanda ya fara fama da wani matsanancin ciwon ciki daya danganashi da asibiti. Bai fahimci bayanan da aka yiwa nanay ba,amma tun sannan yake samun wani irin kulawa daga wajen nanay. Ja a jiki,yawan gaya masa yaji tsoron Allah,yadda zai kare mutuncinsa dana mahaifansa. Sannu a hankali ya fahimci nanay ta sanshi.....ta sanshi sani irin na kar da kar.....ta sanshi irin sanin da uwar da tasan kanta ne kawai takewa yaronta. Tasha ajiye masa litattafai da suke magana akan illolin zina kowacce iri,tasha zaunar dashi ta masa wasu tambayoyi da yakanji kunya qwarai.....amma daga sanda ya soma mallakar hankalinsa......daga sanda ilimin addini ya ratsashi sosai sai ya fahimci yadda zai bawa kansa kulawa,yadda zai kare kansa daga kowacce irin illa ta zina. Tun daga sannan.....tun daga wadannan shekarun ya tsaya akan azumin litinin da alhamis.....tun daga sannan ya sake nesanta kansa da kalar kowacce mu'amala data hada da mata a ciki,kowacce iri ce idan bata zama dolen dole ba. Daga sannan ya maida kansa busy sosai akan aikinsa......akan komai da yasan zai dauke masa hankali daga kowanne tunani na diya mace. Ya sake cusa kansa akan cases masu hadari da wahala sosai a national intelligence security service saboda ya samu ya nisanci kowanne tunani. Yana da burikan da yakeson cimmawa tukunna.....yana da tsarika masu yawan gaske da barin mace ta shiga rayuwarsa a wannan lokacin karyewarsu ne kawai. Bai taba ganin halittar kowacce d'iya mace muraran irin haka ba kaman yau......shi daya yasan da yadda yayi controlling qafafunshi suka dawo dashi daki.....shi daya yasan da yadda yaketa kokawa da numfashinsa.....idanunsa da yakejin wani abu ya cika masa su. Ya isa gaban dressing table din dake dakin,ya xube dukka hannayensa akai gami da sadda kansa yana qoqarin daidaita nutsuwarsa da numfashinsa dake masa wani wahalan zuqa da daidaituwa cikin hunhunsa. Idanunsa a lumshe suke sosai,saidai still hotonta gake gani a ciki,ya dunqule hannunsa guda daya ya daki dressing table din yana kiran sunan Allah. Ji yake kaman hankalinsa zai rabu da gangar jikinsa.....ji yake kaman ya koma.....kaman ya koma ya sameta.....ya rungumeta cikin jikinsa da yanayin da zata mannu sosai a qirjinsa. Ji yake kaman yaje ya kamota cikin jikinsa ta kuma tabbata cikin jikin har sai abinda yakejin ya lafa. A daidai wannan yanayin da yake ciki ta fado fadin. A gigice take,gigicewar da bata barta ta lura da halin da yake ciki ba,sai kawai qoqarin riqo hannunsa da takeyi tana magana a rude. "Falaak......falaak tace zai kasheta.....don Allah ka taimakeni muje....kada wani abu ya sameta". Duk da a rude take amma shi a tsaye yake cak......a tsaye yake cak yana binta da kallo,a tsaye yake kaman an dasashi yana bin sassan jikinta da kallo,yadda take maganan tana girgiza hannunsa sai ya zamana kamar suna suna motsawa ne don su nuna motsin da take ya isa har inda suke. "Ya salam.....ya Allah.....wai bata gani ne ba?,bata fahimta?" Ya fada yana jin 'yar guntuwar nutsuwar daya soma kokawar samowa tana silalewa. "S’il vous plaît(please)" Ta qarasa fada tana riqe hannunsa da kyau har tana shigewa jikinsa ba tare data ankara da abinda takeyi ba. "Najiiiiiii" Ya fada yana fusgar kalmar da qyar gami da dan tureta kadan daga jikinsa yana jin kamar zai zauce tafukan hannunsa akan kunnensa duka biyun kamar wanda numfashinsa ke shirin daukewa. _busy,sorry please_🙏🏽 *zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 08187255862 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 08187255862 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽 💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 31* Turetan da yayi sai ya sanya taji a ranta kamar yanaso ne yaqi kaita. Tsoro takeji sosai......zuciyarta bugawa takeyi,tana tsoron wani abu ya samu falaak. Falaak ce fa?,jininta,ita kadai ta rage mata a yanzun,bata da wani makusanci kamar falaak din a yanzu. "Pleaaaaaaaseeeee" Ta sake fada hawaye suna gangaro mata tari da sakewa hannunsa mugun riqo tana kuma shigewa jikinsa,duk a qoqarinta na amintar dashi ya kaita. "Sub.....hanallah" Ya furta labbansa suna motsawa,numfashinsa yana fita a rarrabe. Kusancinta a gareshi wani irin sake haukatashi yakeyi. Wai ita bata gani bane?,bata gani?,bata lura da idanunsa?,iya idanunsa kadai shi kansa yasan tarin fitina ce da babu ruwan kasheta a nan kusa. "Don Allah" Ta fada a wani irin narke daidai da yadda takejin zuciyarta ta karye. "Kisa fa......kasheta tac......" "Nima kasheni kikeyi........kasheni kikeyi biftuuuuuu" Ya katse numfashinta da maganar da batakai ga qarasawa ba da wani irin birkitaccen sauti tana riqe fuskarta cikin dukka tafukan hannayensa gami da matso da fuskokinsu dab da juna. Cak zuciyarta ta dakata da bugu na wucin gadi kafin ta koma aikinta da wani mahaukacin gudu na wuce sa'i. Wani zazzafan numfashi da yake sauke mata saman fuska shine abu na farko daya fara sanyata dawowa cikin hayyacinta. "Kina kasheni nima......don Allah......" Sai kuma ya kasa qarasawa saboda hannuwanshi da suka dauki rawa. Blue eyes dinta ta fiddo waje,har yanzu tunaninta baikai can ba,saidai wani yanayi na tsoro daya d'arsu a ranta jin yadda tafukan hannuwanshi ke rawa jikin fuskarta. Hannunta daya ta dora saman nashi tana riqewa sosai. "Me nayi maka?,......ban maka komai ba....Allah ban......" "Kinmin biftuuuuuu......kinyimin mana" Yayi maganar da sound na rada,yana sake kusanta fuskarta da nashi fuskar,sannan ya hade fuskokin nasu guri daya ta hanyar hade goshinsu da hancinsu guri daya,ya saka daya hannun nasa ya riqe bayan wuyanta sosai yadda ba zata iya qwacewa ba,sannan ya riqe qugunta da daya hannun yana son matso da ita jikinsa ya hade kusancin dake tsakaninsu. Sai a sannan jikinta ya dauki kyarma,kusancin ya fara mata yawa......iya numfashinsa da suke musaya ta bashi nata ya bata nashi kadai sai ta jishi da wani irin nauyi da girma ba. Ba wannan ba......sanda taji lallausan tafin hannunsa saman fatar cikinta......wani irin zabura tayi,zaburar data raba fuskokinsu saidai bata kawo tazara ko qanqanuwa a tsakaninsu ba. Still bai saki wuyanta ba,hannun nasa tayi caraf ta riqe,sannan ta daga idanunta tana duban qwayar idanunsa. Wani irin abu taci ya hautsina cikin kanta ya daki zuciyarta,wani irin mamaki da tsoro,wadannan manyan fararen idanuwan......wadannan idanun dake da wani irin haske da girma,a yanzun basu taki gani ba. Qananun idanuwa da suka qanqance..... Masu launin ja da wani irin abu a cikinsu daya cikasu taf. Kai yake juya mata a hankali kamar meson yayi magana amma ya kasa,kaman yadda itama ta matsa qaimi gurin riqe hannunsa cikin nata tana juya masa nata kan,sannan ta fusgi.kalmar "A'ah.....a'ah" Dukkanin ilahirin jikinta itama yana kyarma. Idan ta fuskanta,idan kuma ta gane yanason yayi sama da hannayensa ne ta qasan rigar. Saman da zaiyi dasu din kuwa daidai yake da ya sanya hannunsa tsakiyar dukiyar fulaninta?. Wannan gurin?,wannan muhallin da take matuqar tattalinsu?,muhallin da tun daga fara tsiruwarsu bata sake bari koda idanun mammina bare hadimanta yakai kai ba yau shi can yakeson isa. "Aah" Shima ya maimaita fadi mata......kamar akwai abinda yakeson cewa amma bakinsa ya sarqe.....kamar akwai abinda yakeson ya fada amma sam harshensa yaqi bashi hadin kai. Jin yadda ya zame hannunsa a haukace yana ci gaba da tafiya dasu zuwan saman ya qarasa birkitata. "Don Allahhhhhh....." Ta furta tana barkewa da wani irin kuka me dauke da siririn sautin daya dace da lallausar muryarta. Kuka.....wani abu guda daya dake da tasirin karyashi,wani abu daya da baya qauna sam game da diya mace......a yanzun a hankali ya daki kunnensa ya fara karya duk wani lagonsa. "Why?" Ya fada can qasa da wani irin sauti daba lallai ka gane ba sai idan labbansa da sukayi jaa ka kalla. Kamar an yashe tunaninsa da komai nasa completely haka yakeji,baisan yadda akayi ba yadaiji ya fusgota jikinsa sosai,ya mata wani irin mugun riqo,sannan a zafafe ya lalubi bakinta data soma masa wannan kukan dashi ya riqe lips dinta da wani irin salo me taushi amma tafe da zafin nama. A hankali ya soma zagaya lips dinta da harshensa. Yanaso ya dainajin wannan sautin kukanne.....yanaso ta daina cika masa kunne da kukan da tuni zuciyarsa ta yanke kukan sakalci ne. Abinda ya qara adadin yawan rawar da jikinta yakeyi,tayi qoqarin zamewa amma bai bata wannan damar ba,don gaba daya ya sake manneta a jikinsa,ya kuma tura harshensa kai tsaye zuwa cikin bakinta ya fara sauke mata wasu abubuwa dashi kansa baisan yadda akayi ya iya sauke mata su hakanan da zafinsu ba. . Matsanancin tsoro ya dirar mata a sanda shi kuma hankalinsa yayi nisa. Kamar zai hadiye dukka bakin dama komai da komai da yake cikinsa haka yakeji. Yana tunanin samun relief ne......amma sai ya zame masa kamar iza wuta yakeyi da makamashin kara me saurin kunnuwa. Wani irin sound yake sauke mata daya sake rudata ya sanyata tsananin firgicewa. Kuka takeson masa da qarfinta amma bai bata wannan damar ba saboda yadda yake sarrafa bakinta kamar abinda aka halicceshi yayi kenan a duniya. Tsoro ya hanata iya tsaiwa da qafafunta.....yanayin daya shiga ya zare Shima duk wani kuzari nasa,sai gasu suna shirin zubewa qasa warwas,abinda ya taimaka gurin kado da hankalinsa kenan ya sake mata baki da wani irin yanayi me matuqar zafin da idanunsa suka birkice gaba daya kamar ba nasa ba. Sakin da ya yi mata na sakanni su suka bata daman fashewa da kuka tana jin wani abu yana shiga zuciyarta a hankali bayan tsoron. Ta dauka zai saketa ne........amma sai ya hade jikkunansu guri daya da wata irin wawiyar runguma kamar zai ballata gida biyu. Rungumar data bashi daman jin saukar duk wani tudu da kwari na jikinta daya tsone masa idanu......yaji saukarsu sosai a kowanne sashe na jikinsa,abinda ya sanyashi jan waga doguwar ajiyar zuciya kamar zai hadiye zuciyarsa gaba daya sannan ya saki wani irin numfashi kamar zai fidda hunhunsa gaba daya,sannan jikinsa gaba daya ya bada wani reaction kaman an girgizashi kafin yayi collapse a jikinta,kaifi da qarfin rungumar da yayi mata ya soma sassauta a hankali,saidai duk da haka bai saketa ba gaba daya ba. Abinda yayin sai ya d'arsa tsoro a zuciyar akhnan da idanunta suke jage jage da hawaye. Kada taje ko shima ya mutunne ace itace ta kasheshi?. Ta tattara dan qwarin gwiwarta ta motsa labbanta da takejinsu kamar ba'a jikinta ba ta furta. (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) "Ha......haisammmm" Da wani irin sanyi kalmar ta fita a bakinta,sanyin daya sauka cikin kunnuwansa ya sake raunana qarfinsa gaba daya,sai ya zabu sulalewa shi da ita duka suka zube a qasa. Saidai har yanzu fuskarsa tana saman kafadarta,rungumar yakejin kadai yake da ikon yi mata. Bazai taba yin komai da zai zama tilas ko tursasawa ba......kaman ma bai shiryawa wannan abun kai tsaye ba,amma wannan yanayin daya kunnu a dukka ilahirin jikinsa ya mantar dashi komai. Shuru ne ya gifta a tsakaninsu,wani irin shuru daya wuce da komai daya faru,shurun daya sake samar masa da wata kyakkyawar nutsuwa da ya jima bai samu irinta ba. A hankali ya zameta daga jikinsa ya miqe yana jin kamar kansa ya masa nauyi sosai,hakanan qafafunsa sunyi wani irin laushi,kasala yakeji irin wadda bai taba jin irinta ba,so samu yayi koda iya alwala ya koma saman gadon ya kwanta ko yanayinsa zai daidaita. "Ki shirya kafin nayi wanka" Kawai ya fada yana nufar bathroom da wani irin taku da bata taba gani a tattare dashi ba. Da qyar itama takai kanta daki,kunya nauyi da wani irin yanayi da takeji a jikinta suka mamayeta. Zuciyarta ta buga sosai sanda ta tsaya gaban madubi tana kallon kanta. Ashe a haka ta fita?. Ba Brazzier?.....ba dankwali bare mayafi?. Sai yanzu ta gane......sai yanzu ta gane silar komai. Ta manta a haka ta fita......saita miqa yatsanta saman lips dinta tana zagayawa a hankali. Komai yana dawo mata......yadda yayi matan.......yadda ya shigar da bakinta gaba daya cikin nasa kamar zai cinyeshi.......yadda yayi mata wani irin riqo kamar zata karye.......wani yanayi daya shiga daya dimautata........yanayinsa na qarshe da bata fahimci komai a kansa ba "Innalillahi" Ta fada tana jin wata kunya da tunda tazo duniya bata taba jin irinta ba. Ta maida dubanta ga qirjinta,suna nan a tsaye kaman masu gasar nuna kansu,kowanne kana iya ganinsa a muhallinsa daban. "Na shiga uku" Ta sake fada tana waro ido,a haka shima ya gansu?,a haka ya matseta cikin jikinsa?,sai idanunta suka fara tara ruwan hawaye. Tana jin kamar ba zata iya sake hada idanu dashi ba har abada. A ranta takeji shima d'an duniya ne.......haka yake amma sultane yake yabonsa?,haka yake amma ya sani yake sauke idanunsa baya kallon kowa?,ashe haka halinsa yake?. Tunda take ba wani d'a namiji daya taba riqe koda yatsarta ne ballantana hannunta saishi,a yanzun sai takejin kamar wani babban zunubi ta aikata. Ruwa ta sakarwa kanta sosai tana sauke ajiyar zuciya,sai data jiqe jalaf sannan ta saka soso da shower gel dinta ta soma wanke jikinta duk inda taxo saita tambayi kanta ya taba nan?,qila yaji nan gurin.....nanma ya taba?,sai da falaak ta fado mata a rai sannan ta qara hanzarin qarasa wankan nata. Ya jima sosai ruwa yana dukan jikinsa kafin ya soma wankan ibada. Ajiyar zuciya kawai yake saukewa a jejjere kamar yaron da yasha kuka ya qoshi. Ko bayan daya fito tsaye yayi gaban mirror yana duban kansa da kansa. "Alhamdulillah" Ya furta yana motsa labbansa gami da cusa yatsunsa cikin sumarsa. Sake maimaita hamdalarsa yayi. Yana godewa Allah da komai yazo masa in halal way.......yana godewa Allah daya kasance bai taba irin wannan cudayyar da wata mace ba tunda yake a rayuwarsa sai yanxu.... Koma meye halal dinsa ce......ko auren meye dai halal dinsa ce.....mallakinsa ce. Sake duban kansa yake komai yana dawo masa cikin kansa,lallai Allah shine sarki buwayi gagara misali. Lallai Allah ya gama da dan adam. Haka abun yake?,shine abinda yake juyawa cikin kansa kawai,iya haka kawai?,sharar fage?,ya maimaita cikin kansa,sai murmushin da bai shiryawa ba ya subuce masa. Ya godewa Allah daya sanya sirri tsakanin ma'aurata,yayi imanin inda abune da kowa yake gani yau kawai.....a iya haka saisu khadeem sunyi yaga yaga da namansa. "Maleek fa?" Sai wani murmushin ya subuce masa a hankali. A dazun da ya kirashi yana tsakiyar bacci ne,kuma yadda maleek ke magana ya dago aika aikar da yayi. Haushi ya bashi sosai,kuma har yakai mata wayar a wuya yake da maleek din,da burin sai ya masa kaca kaca......amma zuwa yanzun sai yakejin me zaiwa maleek?,mai zaice masa?. Wani yanayi ne daya tabbatar ba wanda ya isa ya cika baki yace zai iya mallakar kansa. A iya haka bai mallaki kansa ba.....baisan ya zata kasance ba idan yakai matakin maleek. *zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 08187255862 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 08187255862 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 32* Kaiwa nan gurin a tunaninsa ya tilasta masa kai tafin hannunsa saman sumarsa ya shafeta a hankali wani murmushin yana sake qwace masa,daya duba lokaci kuma sai yayi gaggawar watsar da tunanin ya jawo lotion dinsa ya fara shafawa. Yanajin wani sakayau cikin zuciyarsa da ruhinsa har ma da gangar jikinsa. Moroccan jallabiyya ya saka fara qal da aka yiwa adon golden zare. Zaka rantse da Allah wani ado na musamman yayi saboda yadda rigar ta zauna masa ajiki ta haskashi ta masa wani irin kyau. Da sassanyan qamshin nan nasa ya zura wasu fararen flip flops sannan ya maida wayarsa aljihu ya fito a nutse. Yana rufe qofan dakin tana fitowa daga cikin dakin itama. Kaman hadin baki ko ra'ayinsu ne yazo daya?. Farar abaya ce a jikinta,ta nade kanta tsaf da mayafin abayan daya kasance yalwatacce ne. Kasancewar abayar fara bai rage koda digo daya na kyan data mata ba,duk da bame duhun kala bace. Fuskarta tayi wani fayau da haske,kaman an sauya mode nata ko wani abu dake tattare da ita tsakanin mintunan da suka rabu kadai. Idanunsa zube akan fuskarta,duka hannayensa suna cikin aljihun jallabiyyan jikinsa,saidai ko sau daya taqi yarda ta kalli ko sashen da yake ma bareshi kanshi. Zuciyarta har yanzu bugawa takeyi,wani tsoronsa takeji yana shigarta,wani kallo na daban take masa yanzu. "Shima ashe haka yake?" Abinda kawai take nanatawa kenan a ranta,don haka ta zabi fara yin gaba duk da tana jin dukkanin idanunsa akan jikinta. Gefan mayafinta taji an riqe,an kuma jawota baya kadan,ta tsaya cak qirjinta yana ci gaba da bugawa,saidai taqi yarda ta waiwaya. "Ki jirani" Ya fada da wani soft tone sannan ya taka zuwa gaban fridge ya ciro gorar ruwa mara sanyi ya cika cup ya shanye. Baisan me yasa da kallonta kawai sai yaji maqoshinsa yana bushewa ba,numfashinsa kuma yana nauyi kadan kadan ba. "Muje" Ya fada yana tsaye daga bayanta kamar wanda aka bawa aikin kula da duk wani motsinta dama fitar numfashinta. Batasan sau nawa yake canza side daga hagunta zuwa damanta ba. Yana hagunta sai ta tsinceshi a damanta,kamar wanda yakejin kariyar da yake bata tayi kadan. Haka kawai yakejin kamar kowa ma kallonta yakeyi,kamar kowa idanunsa yana kanta. Baisan me ya sanya wannan kishin ya qaru a qirjinsa ba,kawai tsaiwarsa a bangare guda yana jin bata gamsar dashi ba. Kamar kowanne lokaci,yanayin na dabanne...... Kusan ko ina ba wani baqon abu bane masoya ne riqe da hannun juna suka kai kawo. Shuru ya ratsa tsakaninsu,shurun daya musu jagora,ya sanya zukatansu tunani mabanbanta. Wani nauyi takeji sosai duk sanda zasu daga taku su sauke tare,wani iri takeji duk sanda taga ya juya ya kalleta sannna ya kauda kai. KUNYA......a yau tasan ainihin zahirin ma'anarta......haka kunya take da nauyi?,duk yadda kallonsa ya zame mata kusan dabi'a a yau dai ba zata iya hada idanu dashi ba. To amma shi daga mode dinsa kansa tsaye yake takunsa kamar komai bai faru ba. Idan ta tuna yadda ya ganta tana jin kamar ta nutse a qasa......tana jin me yasa ta fito?. Idan yadda ya sakata a jikinta ya dawo mata sai taji wani qaramin spark yana tashi cikin jiki da kwanyarta. A tsorace take,mugun tsoron da ba komai take ganewa ba,amma a sanda ya sanyata tsakiyar wannan qirjin.....faffadan kafadar da ta dade da sanin qarfinta......ta kuma dade da zame mata garkuwa game da abubuwa da dama sai da aka sanar da ita shigarta cikin wani sabuwar GARKUWA da bata taba shiga ba a rayuwarta. Swissotel suka isa,sai a sannan ta tuna da iffah. Ta kirata bayan nan har sau biyu sun gaisa,amma basu sake haduwa ba. Batasan me ya faru ba,itadai taji ya cusa zaratan dogayen yatsun nan nasa cikin siraran yatsunta ya kuma hade tafin hannunsu guri daya. "Welcome sir" Abinda ta dinga ji kenan daga bakin ma'aikatan hotel din,tun daga reception har suka kai qofar dakin data shima daya daga cikin manyan suits ne irin nasu,saboda tsarin gurin da komai na dabanne. "Welcome sir" Kalman ya sake maimaituwa a kanta. Wani tsananin mamakin yana sake ninketa. Wato tayi kuskure......tayi kuma underestimating matsayinsa kenan?.....tunda tunaninta ma ya tsaya ne kawai a raffles makkah palace kadai yake da wannan girmamawar?,abun har swissotel ma?.....abun har askar na bakin haram.....WAYE SHI WANNAN MUTUMIN? Ta sake tambayar kanta daidai sanda taji tsoronsa yana sake shigarta,saita yanke zame hannunta cikin nasa tana daga idanunta tare da masa duban rashin yarda. Sake matse hannun nata yayi,sannan ya daga idanunsa a hankali ya zube mata,qwayar idanunsu suka gauraya guri daya. "Waye kai" Ta motsa labbanta zuciyarta na bugawa ta jefa masa tambayar. Ido kawai ya zuba mata kamar baya fahimtar yaren da take magana dashi,sai kuma wannan murmushin da yake narkar da kowacce jijiya dake riqe da zuciyarta ya subuce masa,sannan ya kauda kansa a hankali daidai sanda maleek ke bude qofan dakin. Dole ta janye dubanta ta maida kan maleek din,sai taga yaqi kallonta,idonsa akan haisam. "Fito" Haisam ya furta a nutse yana watsawa maleek idanunsa. Yayi kuma maganar ne ba tare da yabar maleek yace komai ba "Am....amma tana ciki....." "Muna iya komawa ni da ita?" Ya fada yana nuna akhnan da yatsarsa. Sosai ya fahimci abinda haisam ke magana akai,kishi.....kishi ne da bazai barshi ya shiga ciki ba,shima kuma bai yarda ya koma ba duk da matarsa tana ciki. Dole kuma yana buqatar wani,wanin da zai lallasar masa falaak din ya kuma bata taimako bayan wanda yayi iya yinsa. Matsawa akhnan hanya maleek yayi yana fitowa,saidai bai yarda sun hada idanu ba,sai wani gaisuwar babbar yaya da yake mata. "Barka da warhaka tanti.....ina fata kina lafiya" Ita bata ma fahimci wannan abun nasa ba,hankalinta dari bisa dari yana kan falaak,bata taba zaton ta damu da ita ba sai yau,yau din da taji batun kisa. Mamaki kuma ya kamata ganin maleek ya fito gabansu,ba alamun jini ko wani abu na kisa a tattare dashi,kawai tunda taji alamar haisam ya sake mata hannu saita zame da sauri ta wuce ciki. "Fito munafuki" Haisam ya sake maimaitawa yana zubewa maleek idanu. Murmushi kawai maleek ya saki suna takawa zuwa lobby din dake daura da gurin,wanda aka qawatashi da kujerun zama daidai da yadda masu zama a gurin zasuji dadin zamansu. Kai kawai maleek ke girgizawa,ya gaza amsawa haisam kalman munafukin daya kirashi. "Kayyasa......wallahi mun dade a matsayin buhunhuna kuma bahuna......ashe naseeb ya fimu wayo?,me yasa duka shekarun nan muke zaune bamuyi aure ba?" Shuru kawai haisam yayi,da wannan kalar cikakkiyar nutsuwar tasa yake kallon maleek. Yanason gano abinda yaji ba'a kalamansa ba,a yanayinsa da yadda maganan ke fita daga can qasan zuciyarsa. Bazai qaryatashi ba,idan ya gwada da abinda ya faru dazu dashi baisan me ya sanya maleek wannan sambatun ba. Bayason jin komai,kamar yadda yasan maleek din shima ba fada zai ba,amma sambatun da yake masa yayi yawa,yana tsoron kuma amanar sultane a hannunsu,kada yaci gaba da tafi da falaak din a haka,shi yasan illar da irin hakan yake haifarwa a matakin farko tsakanin ma'aurata. "Wanne irin rashin imani ka gwadawa d'iyar mutane?,kanason taci gaba da gudunka?" Sakin baki maleek yayi ya zubawa haisam ido. "Captain......anya kuwa kaje inda naje?" Tambayar ta dan zowa haisam da nauyi,sai kawai ya lumshe idonsa ya budesu duka akan maleek,don ya sani,idan bai sauke masa nauyi me yawa ba daga cikin idanunsa ba yanzun sai ya sauka daga kan layi ko shi ya saukeshi. "Ba wannan na tambayeka ko nace ka tambayeni ba.....ba huruminka bane" Idanun sunma maleek nauyi yadda aka saba,ya dauke kansa zuwa gefe saboda a yau dai yana jin bazai fasa yiwa haisam tsiya ba ko bata da yawa "Allah ya sani ni bada niyya bane,bansan ma yadda akayi komai yazo a haka ba.....amma dai yadda kamin tambayar nan ne captain sai ake gayamin bakaje ko ina ba shi yasa ka tuhumeni,inda ka bude littafin kayi karatunsa da kyau Allah ba zaka tuhumeni ba,saboda kaima......" Saukar wani irin duka a gadon bayansa ya dakatar da jawabinsa,koda ya waiwayo sai yaga haisam ne,kuma sake mulmule hannunsa yakeyi,ba shiri ya matsa zuwa mazaunin gaba (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) "Fisabilillahi ina kan sharafina zaka tsugunnar dani....." "Gwara ka tsugunna din ai......kaga sai kuyi jinyar,tare mara imani" Dariya maleek ya fashe sosai dashi "Um....um fa captain.....kada lokaci yayi muzo muna wasan 'yar buya fa?". "Wasan 'yar bacewa zamuyi" Ya fada yana danna masa harara,dole maleek ya sake sakin dariya sosai yana duban haisam. Qafafunta har rawa suke sanda ta isa bakin gadon dake a yamutse kamar na 'yan dambe. "Falaak" Ta kira sunanta muryarta tana rawa ta kuma haura gadon da sauri tana rarumar falaak din. Rungumeta tayi sosai a jikinta,ita kuma falaak din ta saki kuka sosai tana riqe akhnan din itama. "Me yayi miki falaak.....me yayi miki?" Tambayar kawai da akhnan din ke iya maimaitawa kenan a rude tana sake riqe falaak sosai cikin jikinta. Idanunta akan fuskarta da taga ta wani rame lokaci daya ta fada sosai. "Ba komai" Amsar da falaak ta iya bata kenan. Batasan yadda zata mata bayani ba,batasan me zatace mata ba,saida tazo sannan takejin wata kunyarta tana danneta,damuwa da rudewar kuma data gani tattare da akhnan din saita qara mata qaunarta sosai. Tambayar duniya amma amsar falaak itace ba komai,dole akhnan ta saketa a hankali tana fadin. "Na baki ruwa?,bakinki kaman ya bushe....jikinki da zazzabi sosai". "Wanka nakeso na sakeyi,ruwan dumi nakeso sosai" Kai akhnan ta daga mata jikinta har yanzu rawa yake,don bata gamsu da abinda falaak ta fadinba,bata taba ganinta cikin wannan yanayin ba duk da ba wata doguwar alaqa bace a tsakaninsu. Hannunta ta dauke da dan sauri jin ta dorashi saman wani danshi danshi.. "Jini?!" Ta fada a rude tana duban falaak,saita sake maida idanunta akan bedsheet din. Nan gurinne kawai keda jinin,amma akwai wasu gurare da ya danyi staining kadan kadan. "Falaak......ki fadamin ne yayi miki....jini fa nake gani,ki fadamin ko na kira sultane yanzun nan" "Ba komai.....ba komai tanti" Falaak ta fadi idanunta suna rau rau da hawaye. Ido ta zubawa falaak ranta yana baci,da alama yarinyar soyayya ta rufe mata idanu ne har bata ganin laifinsa,ita kuwa ba zata bari ba.....ba zata bari kowa a cikin su ya cutar dasu ba don suna ganin ba qasarsu suke ba,kawai saita sauka daga saman gadon da hanzarinta,don ta tuna wayar haisam din ya zameta a hannunta sanda zasu shiga elevator. A nutse ya daga idonsa daga kan waya ya maida kanta sanda take fitowa daga dakin,ya zuba mata idanu ganin tana waige waige. Miqewa yayi tsam,don shi kadai ne a gurin,maleek ya sauka can first reception zaya karbi saqo. "Wayata zaka bani" Ta fada tana miqa masa hannunta. Hannun yabi da kallo,gefan hannun rigar tata ya danyi stain na jini kadan. A nutse ya sauke kallonsa cikin qwayar idanunta. Yana karantar wani fushi da zafi sosai cikin idanunta "Kiyi me da ita?" Ya tambaya calmly. *zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 08187255862 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 08187255862 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 33* "Na kira sultane.....na fada masa jini har a kwancinta amma taqi gayamin abinda yayi mata....bayan dazun zai kasheta tacemin" Tayi maganan tana sauke numfashi da alamun fushi sosai a fuska da muryarta. Wani irin kyau tayi masa.....wani irin kyau daya sanyashi lumshe idonsa sannan ya budesu dukka akan fuskarta. Bai taba ganin fushinta na gasken gaske ba sai yau.....wani irin kyau fuskar tayi yadda ta tsuketa. "Ba zata gaya miki ba.....kema ba zaki kira sultane ba....kije ki taimaka mata kawai ya isa". "Jini fa a jikinta?,sannan kace kada na kirashi?" Ta qarashe fada tana kallon yadda yake takowa inda take yana rage tazarar dake tsakaninsu. Bata matsa baya ba,saboda ranta a bace yake da gaske,wannan ya basu daman tsaiwa sosai gab da junan da cikakken motsi dayansu yayi yana iya cike gap din. "Sun cika aurensu ne.....zaki fallasa sirrin first night din wasu ne?" Dummm taji kanta yayi mata,hannunta dake pointing wani guri ya tsaya cak ya qame a gurin. Wani irin yanayi me nauyin gaske ya saukar mata,shin me yasa ma ta tsaya bata ja baya ba sanda yazo dab da ita,gashi yanzu ya fada mata wasu kalmomi da nauyinsu ya sanya takejin kamar ba zata iya daga qafanta ba. "Uhmmm.....tell me....me zakice da sultane din idan kin kirashi,I’ll help you call him." Ya fada yana latsa wayarsa kamar me nema mata number sultane din. Kaf energy dinta aka kwashe,idea dinta kuma ta bace. Shi baida kunya fisabilillahi?,meye na gaya mata haka kai tsaye?,saita samu kanta da kallonsa kawai bakinta ya gaza cewa komai. Sanda ya dago idanunsa sai suka hadu da nata,ya dage giransa dukka biyun. "You keep staring......uhmmm tell me me zaki gaya masa?" Idanunta ta sauke da wani irin sanyi,sai tayi taku uku baya cikin dabara,sannan ta juya da wani zafin nama tana arcewa cikin dakin. Da kallo yabi bayanta,yadda take saurin kawai zai gaya maka akwai abinda ya tilastata,akwai abinda kuma take gujewa,amma sam saurin baiyi matching character dinta ba. Baisan ya akayi murmushi ya subuce masa ba,ya ciji gefan lips dinsa na qasa,ya koma da baya a hankali ya zauna bayan ya ajiye wayar a gefansa. Ta dade tsaye tana kallon falaak sannan ta tattaka tana mata sannu. Tsoro sosai ya dinga mamayarta sanda taga falaak din na takawa da dabara zuwa toilet. Abinda bata taba ba,yau itace da yaye bedsheet da kanta,bedsheet din data ji qwalla da tsoro sun kamata da taga ragowar jinin da yayi staining a jiki. "Maza basu da imani" Ta samu kanta da fadi itakam ta yaya ma zata bari akai wannan abun bare har ayi mata irin wannan aika aikar?. "Kina da tabbaci?" Zuciyarta tayi mata tambayar data kusa tsayar da bugun numfashinta saboda tsoro. Ita ta taimaka mata da iya abinda zata iya ta gasa jikinta,saidai ko gurin gyara gurin falaak din ta lallaba tayi. Koda akhnan batayi mata komai ba zuwanta ya bata relief sosai. Kallon falaak kawai take jikinta a sanyaye tsoro yana kamata,to amma sai take samun sassauci idan ta tuna ba wani soyayya bane a tsakaninsu da zai kaisu ga wannan,uwa uba ma daki daban daban suke kwana,ba kaman falaak ba data lura suna sharing daki daya ne. "Ke kinsan haka yake,me ya kaikai sharing daki dashi?" Tambayar ta bawa falaak mamaki da dariya can qasan ranta,da gaske akhnan batasan haka abun hake yake ba?,inde haka ne kuwa akwai qura,sai ta yanke tayi mata gwari gwari kawai. "Haka abun yake tanti....haka kowacce mace takeyi" "Take uban me falaak?,kinsan me kike fada kuwa?" Ta fadi har batasan tayi spark ba saboda wani tsoro da falaak din ta qara mata. Qasa tayi da kanta dariya nason qwace mata amma tana dannewa. Da gaske koda akhnan tasan da wannan abun amma sam bata taba kawoshi a lissafinta ba sam a cikin aure. "Da gaske nake....ki kira tanti hairaaan kiji" "Akanme?.....ni bazai faru dani ba bare na nemi sani,kema Allah ya baki lafiya ke kika jama kanki" Ta fada tana yamutsa fuska. A yadda taga falaak din a yamutse saboda abu qwaya daya tak ita saita bari ya faru da ita?. "Duk fa wayon amarya sai ansha man ta.....kin manta?" "Falaak.....ki kama kanki" Ta fada tana tsumewa "Inacan tausayinki kamar zai hallakani,amma ke alfahari ma kike da abun?". Ta fada a qufule "Dole nayi alfahari mana....nakai mutuncina gidan mijina,mijina na sunnah ne ya karbu budurcina abun alfahari ne yaa biftu,ina fata kema ya faru a kanki zakifi fahimta" Ta fada a ranta amma a fili sai tayi qasa da kanta tana cewa. "Kiyi haquri na daina" Knocking akayi aka turo ana shigowa,maleek ne,sai a sannan akhnan taga basarwar da yaketayi,sai yanzu ta fahimta "Mugu" Ta fada qasan ranta tana jin haushinsa yana saukar mata. Wayarta ya ajiye mata a gefe yana cewa. "Captain yace ki duba akwai saqo". "Captain?" Ta maimaita tana daukan wayar,don sunan baqo ne a kunnuwanta,bata ma kuma gane wanene ba. Procedures ne na yadda falaak zata samu relief a rubuce cikin wayar ya rubuta ya ajiye a notebook dinta. Kunya taji ta kamata sosai gauraye da haushi,har shima wai yasan meye ya faru ne?,kawa saita dan kai idanunta kansu maleek. Yadda ya gwaggwafe gaban falaak din riqe da yatsunta yana murzawa,har ita dake gurin bata iyajin abinda yake gaya mata ya aza mata nauyi da yawa,kawai sai taji ba zata iya zama ba,ta miqe tsam,daidai sanda yake fadin. "Tanti....ki zauna fita zanyi" "No" Tace a taqaice kawai tana takawa gami da ficewa a dakin. *_A G A D E Z_* *_SULTANE PALACE_* Zaune take a gabansa cikin nannauyar kwalliyar na dake cike da alfahari da kuma nuna isa,kwalliyar data qara adadin nauyinta don ta boye ramar data fara yi wadda ta bayyana kadan har a qasusuwan wuyanta. Tun daga watannin baya,ranar da gobara ta tashi a gidan. Bacewar tamim.....bacewar yalwa,gobarar villa dama dauki daidai din da akewa hadimanta,har xuwa ranar qarshe da 'yan jarida suka dirar mata bata sake baccin kirki ba. Kaman zatayi sanyi,kaman zatayi collapse,kaman zata saddaqar amma kuma zuciyarta ta gaya mata KI TASHI ZAITUNA!. Wani irin salo take gani tattare da yaron da dawowarsa yafi haihuwarsa zame mata barazana a rayuwarta. AHMAD yaron data kowacce fuska baka isa ga qaryata jinin sultane bane a jikinsa. Bai rayu dasu ba....bai rayu cikin masarautar ba......amma yasan kowanne nau'in salon sarautarsu.....lungu da saqo na cikin gidan.....adadin ma'aikata dama komai dake wanzuwa a cikin gidan. Batayi mamaki ba.....kasancewar ALSAAMIT tattare dashi zai iya zama mafi girman hatsari fiye da haka. (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) Wani irin takawa d'ai d'ai taga kaman morsa safiyya tanayi.....wani irin girma ta fuskanci kanta yanayi......abinda ya hanata bacci darare da yawa.....saidai kuma ta samu babban makama sanda ta soma lura da rade radin da kuma gani da tayi da idanunta SULTANE bashi da wani cikakken qwari da lafiya. Murmushi tayi sanda ta lura da wannan "Wataqila ina da sauran dama ne.....daman da zata zamemin ta qarshe" Ta kama damar da kyau kuwa,ta fara kusanta kanta da sultane matuqar kusantawa. Abinda ya bata mamaki yadda take samun cikakken dama da access da komai,saidai cikas kadan kadan da take samu daga ahmad din. Yaron da idan hanya ta hadasu yake mata wani irin kallo,kallon data tabbatar idan har yana da dama.....idan har zai yuwu zai iya daukan wuqa ya kaita lahira. "Ta yaro kyau take bata qarko..... Ka daina dariya wasa yayi kyau.....wannan zaqin mulkin......wannan darajar da wannan matsayin gaba daya na 'yan kwanaki zuwa watanni ne....zaka sake bacewa bacewar da har abada ba zaka dawo ba" Haka takan fadi cikin ranta,amma a fili saita bishi da murmushi. Kamar yanzu da take zaune gaban sultane din,tana yanka masa fruit din tana bashi yana sha,tana kuma jansa da hira a nutse. Tun daga nesa ta hangesu,morsa safiyya ce cikin wata irin shigar kamala dake bayyanar da darajarta da wani irin Kwarjini. Ahmad yana biye da ita a baya da wani kalan girmamawa tamkar yana fadawa duniya ITADIN MAKWAFIN MAHAIFIYATA CE. Ta zuba musu idanu da gaske,har cikin tsakiyar zuciyarta tana jin wani irin zugi a duk sanda ta gansu a haka. Dawowarsa ta sake qarawa morsa safiyya wani irin girma da martaba da bata zata ba,saboda kowa kiranta yake UWAR YARIMA ME JIRAN GADO. Duk kuwa da yadda taso sunan ya zamana nata ne.....ko ta hana tasirin sunan,amma ko daya a ciki bata samu nasara ba. Akwai tarin mutane masu yawan gaske dake neman kusanci da Ahmed din,wanda kusancin yana da muhimmancin da dole kowa ya buqaci wannan gurbin a kusa dashi. A zahiri saita saki fuskarta,tana maida dubanta ga sultane da bai lura da tahowarsu ba. "Ga magaji nan zuwa shida mamarsa". Kansa ya daga zuwa sashen,yana duban Ahmad yana jin wani abu me girma yana motsawa cikin zuciyarsa. Baisan dame zai yiwa haisam sakayya ba....duk da har yanzu baisan yadda komai ya kasa ce ba har yanzu. Murmushi kawai yake saki har suka iso,murmushin da mammina take jinsa kamar tsiruwar allura saman naman zuciyarta. "Barka da hutawa" Morsa safiyya ta fada tana cire takalmanta a girmame tana qarasowa gabansa. "Bakanki uwar yarima" Murmushi ya subuce mata tayi qas da kanta,yanayin da ya masa kama sosai da safeena. "Da kanka me martaba?" "Sunan ya dace da wadda aka bawa ai......ga maman gimbiya....ke kuma ta yarima ce" Ya fada yana nuna mammina data qaqalo murmushin dole. Idanu morsa safiyya ta daga ta kalli mammina,cikin sa'a ita ita take kalla,sai kawai safiyyan ta ajewa mamminan murmushi tana dauke kanta. A yanzun bataga komai tattare da mammina ba sai wata kwantacciyar damuwa,damuwar da duk dare saita tsaya saman abun sallah ta kaiwa Allah sunanta. Allah ya hanawa rayuwarta sukuni muddin da haqqin safeena saman wuyanta. "Zamankin nan a gabana.....sai naga kaman safeena ce" Ya fada zuciyarsa tana masa nauyi. *zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 08187255862 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 08187255862 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 34* "Allah ya tsinewa safeena da kabarinta dama dukkan abinda ya fito ta tsatsonta dama ahalinta gaba daya" Mammina ta fada har bakinta yana motsawa,wani abu me masifar nauyi takeji yana sauka saman zuciyarta. Ta tsanu safeena tsana mafi girma,tsanar da ko a lahira batajin zata daina mata wato bayan an mutu an gama kwanciyar kabari an tashi,dukkansu basu kai su goge wannan tsanar ba. Ba wani dan adam a duniya daya taba kawo ma komai nata cikas sai ita.....ba wani wanda ta taba saka plan a gabanta ya zama silar wargajewarsa bayan baqar wahala datasha akai irinta. Daga ita sai IBRAHEEM,sauqinta daya.....IBRAHEEM har yanzu yana cin darajar taba sonshi da zuciyarta tayi,amma duk da haka shima saida ta barwa rayuwarsa tabo ta hanyar daukar rayuwa d'a na farki daya soma haifa a rayuwarsa. Taimakonta daya sautin maganan da tayi baikai ga fita ba,saidai ahmad da idanunsa suke kanta ya tabbatar akwai wani abu data fada. Murmushi morsa ta sake. "Allah yayi mata rahama" "Ameen amee" Ahmad da sultane suka hada baki gurin amsawa. "Ya qarfin jikin?" Ta sake tambayarsa "Mun godewa Allah dai" Yadda yayi maganan sai morsa safiyya taji zuciyarta ta tsinke. Yanayin yadda safeena ke gaya mata kenan a kullum rana har ranar data bar duniya. "Allah ya baka lafiya madawwamiya kai da sauran marasa lafiya" "Ameen" Dukkansu suka amsa harda mammina a wannan karon wadda zuwansu gurin ya sanya taji kaman ta zama bare,kaman an wareta. "Yarimanmu" Mammina ta fada tana murmushi. A nutse ahmad din ya juya yana dubanta,ya aje mata wani kallo da yanayin izzar data taba mammina din sosai. "Wai duka yaushe ya iya wadannan abubuwan gaba daya?" Ta tambayi kanta da kanta. "Idan kina fada,kaman kina qarawa zuciyarki nauyi ne,inda kin haqura da furtawar kiji da abu daya". Ya fada da yaren oromo daya tabbatar ba wanda zaiji abinda yace,don ko morsa safiyya ya fahimci ba yaren kowanne bangaren takeji ba,tsahon barinta qasar kuma yasa ta manta wasu abubuwa da yawa. Murmushi kawai ta maida masa kaman yadda ta saba,har yau ko kalma daya bata taba furta masa ba,amma kuma shi ya sani,hakan ba yana nufin komai lafiya ba. Gaban sultane ya qarasa cikin girmamawa ya tsugunna. "Muna da baqi ranka ya dade cikin gidannan" "Baqi?,wadanne iri?" Sultane ya fadi,don yadda yakejin jikinsa a yanzun bacci kawai yake da buqata. "Eh baqi.....amma kamar ba gurinka kai tsaye sukazo ba.....daga babbar hukuma,alhaji nasiruddeen bahago" Jin sunan kawai ya sanya sultane tashi ya zauna sosai. "Ba baqi bane ahmad....akwai sanayya me girma,duk sanda kuma kaga sunxo babban dalili ne ya kawosu,a shigo dasu" Ya fada yana duban Ahmad din. Kai ya jinjina a nutse,ya miqe wani sirrintaccen murmushi yana fita daga fuskarsa......ya taka a hankali xuwa qofa don bawa me wada umarni. Tunda suka shigo gurin idanun mammina yake kansu. Haka kawai takejin akwai wani baqon al'amari a tattare dasu. Yadda suke dan kallonta daya bayan daya lokaci taji bata nutsu dasu ba. Bata duba yadda morsa safiyya ta kame daga gefe ba,suka gaisa cike da kima da dattako,suka kuma duba jikin sultane sannan suka mata barka da dawowar Ahmad ba tace. "Kaman buqatar kwanciya sultane yake....don Allah idan ba matsala,ko zaku iya gama komai da wuri ya samu ya huta" Ta fada tana miqewa. "Zaki zauna ne ai hajja zaituna,zuwan naki ne" Alhaji nasiruddeen ya fada a girmame. Cak ta dakata tana dubansa,saidai kafin tace komai ya maida dubansa ga sultane. "Allah ya baki yawan rai,ayimin afuwa nayi magana da iyali kai tsaye ba tare dana nema izini ba" Murmushi kadan sultane yayi,ba jiya ba yau ba,shekaru masu dama ne suka bada sanayyarsa da sabonsa da Alhaji nasiruddeen da kuma yanayin aikinsu. "Ba komai......zaituna....zauna" Ya fadi yana dubanta. Murmushinnan ta qaqalo,sannan ta koma tana zama din,a qasan ranta tana fatan wani abu ne ya taso wanda zai kuma daga darajarta. "A daren shekaran jiya hukumarmu ta kama wasu mutane......wanda nasan labarin ya iso gareka?" Kai sultane ya gyada a nutse. "Ma sha Allah.....munyi magana dasu,mu tuhumesu,mun kuma matsi bayanai muhimmai daga gurinsu,saidai ba yadda muka iya.....duk yadda mukaso mu kauce sunan iyalinka ya fito a ciki". Magana tasa ta qare da wani irin shuru......sannan kuma ta jona wani burkitaccen yanayi a zuciyar mammina da kwanyarta. "Iyali waye a ciki kenan?" Tayi tambayar da sultane ya buda baki da zummar yi. "Hajja zaituna,giwa". Ba wanda wuta bata daukewa a gurin ba,banda Ahmad da yake zaune abinsa yana gyarawa sultane rigar jikinsa. " Ayi mana afuwa" Alhaji nasiruddeen ya fada yana sadda kansa qasa. Shuru sultane ya sakeyi,mamaki kuma yana dan cikashi. Me ya hada iyalinsa dasu?,me ya hada zaituna kuma da Office Central de Répression du Trafic Illicite des Stupéfiants(hukumar hana fataucin miyagun qwayoyi). Ajiyar zuciya ya sauke,yana maida idanunsa kan mammina. "Kina da abinda zaki ce?". Kai ta juya kadan,tana qoqarin danne komai da komai da takeji. Ida aka ajiye komai ma.....ita giwa?....mace kamarta ace an shigo har masarauta bincike a kanta?. " Bani da abinda zance.....kawai abinda zuciya da jikina suke gayamin shine......an shirya tozartani ne....ta yuwu an hada baki da abokan adawa don a bata sunanka dana masarautarmu gaba daya" Ta fadi tana fatan maganartata tayi tasiri a zuciyarsa. "Ba haka bane Allah ya baki yawan rai...." Alhaji nasiruddeen ya fadi don kare zargin da takeson jifansu dashi,saidai kafin suce komai sultane ya dakatar dashi. (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) "Duka wannan bata taso ba,basuce komai a kanki ba,hasalima basuce suna zargi ba,bincike kawai zasuyi don wankeki daga zargin da wadancan mutane suke jefa a kanki,so indai hakanne bana tunanin zai zama wata damuwa......." "A shiga har gidana.....na aure da wasu garada....ayimin bincike har inda yake sirrina ne sannan na gaza damuwa?". " Ba irin wannan binciken bane,amintattunmu ne guda hudu kawai " Alhaji nasiruddeen ya fadi da girmamawa. Daga kanta tayi ta zube masa idanunta a kanshi. Taso ta ganeshi,koma tace ta ganeshi,kuma daga wannan aikin batajin zai sake gigin yin wani aiki daya shafi koda na qasanta ne ballantana ita. "Na fahimta.....na fahimta da kyau,ba kuma laifi,kuna iyayi" Ta fada tana gyara zamanta sosai da yanayin saukar nutsuwa a zuciyarta. "Mun gode" Shima ya fada yana rusunar da kansa. "Zaki zabi da wanda zasu shiga cikin hadimanki?". Kai ta girgiza tana murmushi. " Ba zabi.....suna iya shiga da duk wanda suka zaba". "Ahmad......ka rakasu" Kiran sunan ahmad din kawai sai daya kada hantarta. Me yasa ahmad?,me yasa ba zaa saka wani ba ahmad ba?,ahmad daya rayu cikin wata rayuwa data bashi experience din da ko jami'an bata jin suna dashi?. Da idanu ta bisu har suka kammala ficewa gaba dayansu,duk da wani sashe na zuciyarta yana cika da wani irin confidence. Duk inda suka gilma cikin gidan sai idanu sun bisu. Baqon abune ganin ma'aikatan Office Central de Répression du Trafic Illicite des Stupéfiants tsakiyar masarautar haka suna tafiya kansu tsaye,tafiyar ma kuma bisa jagorancin yarima ahmad muhammad hammud. Ba wannan ba.......yadda suke dosar sashen mammina kai tsaye sai abun ya zama wani daban,abun kuma yaja hankulan duk wani hadimi dake kusa,wanda ke nesa ma labari ya fara tsalluwar masa. Wasunsu suka fake da ayyukansu,wasu kuma suka nemi guraren da suke da tabbacin duk abinda ya faru zasu iya samu masaniya. Duk da yawan securiy dake kula da kowacce qofa da zaka sanya qafarta ta sassan mammina,amma babu ta inda suka samu tuhuma tambaya ko kuma tsaiko saboda yarima ahmad dake tare dasu. Alhaji nasiruddeen ya gyada kansa a hankali. "Me yasa girma yawan adadin masu tsaro na sashen nan ya ninka na ko ina?" Yayi tambayar yana duban fuskar ahmad. Kafadarsa ya daga kadan "Bazan ce ga dalili ba,don kusan nima har yanzu baqo ne cikin gidan" Ya bashi amsa akan salo da tsarin da aka dorashi tun farko yayin magana da baqin fuska. A katafaren parlor dinta suka fara aikinsu,mutum hudun nan gaba daya Ahmad na biye dasu cikin qwarewa. Suka kammala da parlor din farko,suka wuce na gaba,daki bayan daki....parlor bayan parlor har suka dangane da dakin baccinta na qarshe wanda ya zama na musamman a gurinta. Komai sai da suka bincike,suka kuma kara masa na'aura,saidai ba wani abu daya basu haske akan abinda suke tuhuma ko kuma nema. "Muje kawai" Alhaji nasiruddeen ya fadi cikin sarewa da rashin qwarin gwiwa. Taku biyu Ahmad yayi yana shirin sanya qafarsa waje idanunsa suka sauka kan wata waya data shigo ta window din dakin. Tsawa yayi cak yana qare mata kallo,wani abu daya taba faruwa a rayuwarsa ta baya yana dawo masa. "Kai!....zo nan" Ya kira tamim,wanda shi ahamd ya zaba aka hadosu dashi. daurewa kawai yakeyi......amma kowanne sashe na jikin tamim rawa yake. "Gani" "Wannan wayar mece?" "Ta panel ce...." "Panel wanne iri?" "Na Sola" "Meye dalilin biyo da ita ta nan?" Ahmad yayi tambayar yana zubawa tamim idanu. "Panel na solar din gidannan dukka a jimlace suke guri daya....baya ga haka ba wata waya da wani yake iya ganinta da idanu koda ta wuta ballantana solar.......meye dalilin sakawa daki guda daya wayar panel?" Ahmad ya qarashe tambayar yana duban Alhaji nasiruddeen wanda kiran da Ahmad ya yiwa tamim ya jawo hankulansu suka dawo dukkansu. "Ku duba waccar wayar" Ahmad din ya fada yana ratsewa ya wucesu su da tamim din,saboda ganin wayar ya tuna masa wata rayuwa da yayi a baya,hawaye ne cikin idanunsa kuma bayaso kowa ya gani. Yana kan koyarwar haisam koda yaushe. "Namiji duk inda yake jarumi ne,jarumtarka tana ninkuwa sama data saura a sanda aka haifeka shugaba....kuma a gidan sarauta....ko sau daya hawaye bai kamata ya fita a idanun NAMIJIN DUNIYA BA,idan ma ya kama zasu fita din ba'a kan idanun kowa ba". Wannan maganar ya riqe,kuma ta dasa jarumta da yawa cikin ransa. *_Tabdijan.......rugiji gabji.....AIKE NE DAGA ME GAYYA ME AIKI ko kuma ARASHI NE?.....SHIN ME SUKE NEMA?,zasuci nasara su kama abun harinsu?,ko GIWA zatayi nata aikin na tabbatar da faduwarsu?_* *zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 08187255862 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 08187255862 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 35* Idan ya tuna a baya shi din tantirin dan shaye shaye ne.....idan ya tuna a baya yadda ya rayu cikin maye,buguwa da shan kowanne irin nau'in kayan maye sai yaji kaman ya dawo da baya ya goge komai. Denawarsa wani abune da ko iya shi kadai haisam yayi masa bazai manta dashi ba. Wani irin dainawa ta farat daya cikin taimakon wasu addu'o'i daya bashi da wanda yake masa da wanda yake bashi yasha. Cikin sauqi komai ya dinga zarewa daga ransa bayan uban amai da yayi kwanaki uku yana yinsu a jere. Wannan shine ya bashi experience na iya gane gurin da ake ajiyar kayan maye da qwayoyo,yake iya kuma sansanosu. Ya sauke ajiyar zuciya yana furta "Alhamdulillah" (Dama ita rayuwa haka take,duk wanda ya shuka tsiya wallahi wallahi wallahi sai ya girba,ruwanka ka shuka alkhairi ruwanka ka shuka sharri,ta cutar da rayuwarsa da plan din ta ruguzashi......gashi a qarshe shine ya zama silar tonuwar wani birnannen sirrinta da ba wanda ya sani,tayi jifa ya dawo mata). Hand glove Alhaji nasiruddeen ya bawa daya daga cikin yaran bayan dukansu suma sun sakashi a hannunsu. Wata siriryar wuqa yaran ya bude,suka isa gaban igiyar dukkaninsu. Daga qasa suka fara farketa suna fedeta,saidai basuga komai ba. Suna dab da isa rabin wayar wasu fararen abubuwa suka fara bayyana. "Ci gaba da tsinkesu" Alhaji nasiruddeen ya fada. "Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un" Kawai yake maimaitawa. Ba ita ba,darajar sultane yake kallo. Da wanne idanu mutanensa zasu kalli gidan da masarautar gaba daya?. Giwa.....matar sarki guda?. *S U L T A N E* Wani irin shuru ne ya ratsa gurin tun bayan fitarsu Alhaji nasiruddeen zuwa ga binciken,shurun da morsa safiyya taji ita ba zata iya ba,ta sauko gaban sultane sosai ta zauna tana sake masa murmushi. "Ranka ya dade......munyi waya da amarya jiya fa" Kansa ya daga yana jin kalamanta suna sauke masa wani abu. "Amarya?,wacce a ciki?" Murmushi itama ta maida masa. "Yata......'yata akhnan mana" "Sonkai safiyya?" Yadda yayi maganan ya sanyata sakin murmushi. "Falaak dai nabar muku,amma akhnan har abada tawa ce.....kuma tamu ce" Tayi maganan da manufa biyu. Manufar kuwa takai,ta isa inda takeal taje. Daga kai tayi tana duban morsa safiyya,duk da yanayin jira da dako irga mintunan da suke shudewa da takeyi amma hankalinta yana kai. Har akhnan tayi kira?,tayi waya amma ita bata kirata ba?,bata nemeta ba?. Anya batasan waye almaz a gurinta ba kuwa?,banbance babancen suna qara yawa......sauyawar yarinyar haka da sauri yana bata tsoro. Idan har shine yake hure mata kunne.....saita sanyasu dukkaninsu sunyi dana sani. Akan ta kasa nasara a rayuwarta......gwara ta rasa rayuwarta. Bata shiryawa tsaiwa don ta fadi ba.....bata shirya kallon toxarta da idanuwan data tanadesu domin kallon nasararta ba. Da ita dake tunanin,da sultane dake hira a hankali cikin taushi da morsa safiyya magana ta neman iso daga me wada ne ya dakatar dasu. "Sun kammala sun dawo,suna neman izinin shigowa" "A gaya musu su qaraso" Sultane ya fada yana gyara zamansa,morsa safiyya ma tana sake gyara lullubinta. A jere suke shigowa,Alhaji nasiruddeen da kansa yana riqe da babbar baqar leda......babbar baqar ledar da kallo daya tak mammina tayi mata taji wani abu ya karta a mararta jini me dumi taji yana tsinke mata. "Wannan alamace ta tashin hankali.......amma ni zaituna bana taba yarda na fadi" Ta fadawa kanta da kanta, "Bana ja da baya,bana bada kai.....giwa ko ta fadi tafi qarfin wawa" Ta sake jaddadawa kanta tana hadiye wasu abubuwa masu tsananin tauri razani da firgici zuwa cikin cikinta. Gaban sultane ya matsa kansa tsaye ya zubesu yana zazzage ledar. Idanu sultane yabi kayan dashi zuciyarsa tana bugawa,Alhaji nasiruddeen ya koma da baya a nutse ya zauna yana fuskantar sultane. "Bincike ya kammala......kuma zarginmu ya tabbata......ga irin nau'in kayan da muka samu cikin dakin". Zuciyar sultane tayi wani irin nauyi,ba jiya yau ko dazu dazu yasan Alhaji nasiruddeen ba. Mutumne daya qware gurin aikinsa,cikin tarin gaskiya da amana. Uwa uba qasarsa ta niger qasace da take da tsauri akan sha'anin cin hanci da rashawa. Babu ta inda za'a shirya komai saboda cin hanci ko toxarci. To amma abin yazo mata wani iri,ta wata sigar daya kasa yarda dashi. "Ayimin afuwa Allah ya taimakeka......inaso a bani daman yi mata wasu tambayoyi a nan....idan kuma hali yayi zamu wuce da ita zuwa office dinmu" Maganan ta zowa mammina a bazata,wanne office?,ita din zasu dauka don tuhuma? "Na baka nasiruddeen" Sultane ya fada kansa tsaye a sanyaye. Bashi kadai ba,hatta da morsa safiyya a sanyaye take kallon komai. Tafi kowa sanin wacece zaituna kaf fadin agadez,bata tunanin akwai wani wanda zai gaya mata wacece ita......amma wannan lokacin abun ya girme mata itama. "Ranki ya dade......wadannan qwayoyin da hodar iblis......" "Ba nawa bane" Ta amsa kai tsaye tun kafin yakai qarshen tambayar tana qoqarin cusa nutsuwa cikin maganganunta da reaction dinta. Shuru ya ratsa bayan amsar data bayar. Shurun ya zarce na wasu sakanni,sannan ya sake magana. "Amma an samesu cikin dakinki". "Eh ba nawa bane" Ta sake maimaita amsa daya dai. Dole akwai wani yanayi na aiki,da muddin ya biyo ko ta kan waye a danne sanayya,banda ita dince.....ba wanda za'a kama red handed da wadannan kayan a tsaya masa tambaya cikin gida. "Bedroom dinki......dakin kwananki,waye yake amfani dashi?" Yayi tambayar yanayinsa yana nuna mode na aiki ya shigeshi. Idany ta zuba masa itama sosai,tamkar tana gargadarsa,tamkar tana gaya masa cewa. "Kabi a hankali.....ina da hadari sosai". "Nice" Ta amsa kai tsaye. "To me yasa suke cikin dakin?" Ya maimaita. Shuru ya ratsa na sakanni,sannan ta amsa "Ta iya yuwuwa wani ya saka saboda ya batamin suna kamar dai haka" "Wani?.....kamar wa kenan?" Ya sake tambaya yana dubanta ta tsakiyar idanunta. Duk amsar data kamo sai taji ta subuce,akwai sunaye da yawa da takeso ta furta amma sai koda qwaya daya yaqi fita a bakinta,wannan ya sake bada shuru me nauyi,har sai daya sake magana. "Sun kasance cikin wani irin boyo na sirri,da dukkan alamu dake nuna ba'a son kowa yasan dasu,da dukka wata kalar dabara dame laifi yake iya boye kayan laifinsa...." "Kana zargina kenan yanzu?" Ta fada fushi yana nunawa saman fuskarta. Idanu ya zuba mata,yana karantar muddin akaci gaba a nan,muddin yaci gaba da biye mata zata nannade tabarmar kunya da hauka ne,kuma ya tuna,wannan umarnin da aka ruba masa shi da manyan baqi BA'A GABAN SULTANE KOMAI ZAI KASANCE BA. sai ya tausa muryarsa "Ba tuhumarki nake ba.....tambaya ce kawai". Kalmar tasa ta qarshe ta danneta,shurun da yayi mata nauyi da yawa ya biyo baya,kamar an daure harshenta,kamar an daure kowacce kalma daga bakinta,tana jin sanda ya juya ga sultane. " Ayimin aikin gafara ranka ya dade,a bani dama mu wuce da giwa zuwa hukuma mu qarasa bincikenmu a can,idan komai ya daidaita zamu dawo da ita har gida in sha Allah". Tayi zaton zataji muryar sultane yana fadin bai yarda ba,ta dauka zaice sam sam,amma ga tarin mamakinta sai taji muryarsa cikin rauni yana cewa. "An baku izini". " Muhammad?" Ta kira sunan sultane kai tsaye idanunta kafe cikin nasa. Yadda ta kirashi gatsal din ya jawo hankalin kowa da kowa a gurin hatta dashi sultane din. Zare idanunta tayi ta maida kan ma'aikatan daidai sanda sultane yake cewa Alhaji nasiruddeen su dan basu mintuna biyar. Ba musu dukka suka juya suka fice,gurin ya rage daga ita sai morsa safiyya sai sultane din,morsan da sam mammina ta manta da wanzuwarta a gurin saboda tsananin rudewar da taketa pretending tana boyeta. "Kai da kanka ka miqa matarka inda za'a wulaqantata?,da kanka ka amince wasu jami'ai su tafi dani?". Idanunsa ya lumshe sannan ya bude lokaci guda. " Ba tozarci ko wulaqanci bane.....haka tsarin yake,dokar ce a haka,muke gyara doka da bayar da ita.....ba zamu taba zama masu karyata ba.....idan na hana su tafi dake ashe bamu da gaskiya kenan?, a duk inda kake gaskiyarka ce take fidda ka,ita take kunceka ta dawo dakai mataki da matsayinka" Maganan ya mata kama da jirwaye me kama da wanka. Har ta bude bakinta zata sake magana sai idanunta suka sauka kan morsa safiyya,abinda ya sanyata shanye duk abinda take da niyyar fada,ta maye gurbin abinda yake kan fuskarta da murmushi (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) "Na yarda dakai,na amince ba zaka taba sakin hannuna ba a sanda nafi buqatarka. Ko waye ya qulla wannan abun zai warware in sha Allah.......rabuwarmu ko toxartata saidai a jira" Idanu morsa safiyya ta kawar kawai,can qasan ranta abubuwa da yawa suna kai kawo. Ta sani.....zaituna nada wani irin hatsari.....ta sani,zaituna din wata halitta ce da komai akace zata aikata zai farun,sai abinda Allah ya tsare kawai,wadannan maganganun duka ta sani tana yinsu ne saboda ita. Ita da sultane din duka sukabi zaitunan da kallo sanda take ficewa gurinsu Alhaji nasiruddeen. Motarsu suka bude mata,don baya cikin doka mutum ya tafi a motarsa kaman yadda zaituna taso tayi da farko. Inda tuhuma ce kawai ba'a kamata da komai ba ana iya bata wannan damar. Da farko ta tsaya kai da fata bata shiga motarsu saidai ta taho a tata motar,duk da tasan cewa doka bata bata dama ba. Amma sai tawagar 'yan jaridar da sukayo kansu.....'yan jaridar da basusan waye ya kirasu ba suka sanyata da qafafunta ta shige motar,musamman da idanunta suka sauka kan biyu daga cikinsu. Suna cikin 'yan jaridar wancan ranar......suna cikin 'yan jaridar da suka yada labarin takardunta na wancan ranar,har abun yake neman zame mata barazanar da a yanzu ake d'ari d'arin karbar taimako daga gurinta daga kowanne asibiti ko gidajen marayu da sauransu. "Da gaske ne an samu qwayoyi a tare dake......da gaske ne tafiya zakuyi don tuhuma?" Tambayoyin da suka ratso glass din window din da take zaune suka isa ga kunnuwanta,tambayoyin da suka tilasta mata runtse idanunta tana jin zuciyarta da idanunta suna zugi. "Ina tafisu da nace zamu tafi tare?" "Ba'a ganta ba......amma ko daga baya ne zata iskemu a can" Driver din motar ya bata amsa yana tayar da motar. *S U L T A N E* Idanu morsa safiyya ta zubawa sultane,wanda tun bayan tafiyarsu mammina bai sake cewa komai ba banda shurun. Koda ba'a gaya mata ba tasan yanayinsa,tasan kuma halinsa,alamu ne na zurfafa cikin tunani,tunanin data tabbatar baida fa'ida gareshi da lafiyarsa,musamman yanzun da yake yawan qorafi akan yanayin qarfi da lafiyar jikinsa. "Bappin akhnan" Ta kirashi da sunan da tasan yana masa dadi sosai. Kansa ya daga yana dan sake mata murmushin qarfin hali. "Nace ko zaka tafi ka kwanta ne?,zuwa anjima qilan idan ka samu kayi bacci zakaji dadin jikin naka?" Kai ya daga mata a hankali,shi kansa baya marmarin ci gaba da zaman. Wani irin abu yakeji yana taso masa game da mammina. Wani irin yanayi da yafi kama da zargi rashin yarda da rashin aminci. Ya sani,gidansa cike yake da tsaron da ba wanda ya isa ya keta sassan matansa ta sauqi haka har yayi ajiya makamanciyar wannan,ballantana sassan mammina din,da kusan ko sashensa bazai nuna masa tsari tsaro da kulawa ba. "Muje" Ya fada yana yunqurin miqewa. Koda ya miqe sai yaji kamar ana jijjiga jikinsa da qafafuwansa. Sai yaji kamar komai yana shirin bace masa a lissafinsa,kafin ya iya yin komai wani jiri ya debeshi. Salatin morsa safiyya da hailalarta kawai ya iyaji,yana jin sanda ta tareshi amma bata da wannan qarfin,dole ita dashi din duka suka zube a qasa. Da wani irin tashin hankali take kiran sunansa tana tattaba fuskarsa ganin idanunsa suna komawa gami da rufewa ruf. Iyakar yadda zatayi ya gagara,sai ta miqe a birkice tana kama sunayen duk wani hadimi da tasan za'a sameshi a kusa dasu. *zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 08187255862 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 08187255862 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 36* "Ba numfashi a jikinsa kwata kwata" Daya daga cikinsu ya fada yana duban morsa safiyya gumi yana yanko masa. "Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un" Ta samu kanta da maimaitawa sau babu adadi,ya sulale tana zama dab dashi tana riqe hannayensa sosai cikin nata. Safeena ce take dawo mata cikin kanta....wancan ranar da ba zata taba gogewa cikin kanta ba,har sai ranar da tata ta sameta. "Karka tafi ka barni kaman yadda safeena tayimin" Ta motsa labbanta tana fada a hankali tana jin kamar hankalinta yana neman gushewa daga jikinta. "Likita ya iso Allah ya baki nasara" Taji muryar daya daga cikin hadiman,kai ta daga tana dubansa kamar bata ganewa,sai kuma ta sake matsawa kusa da sultane din da har yanzu ba wani abu nasa daya motsa,kamar tana gaya musu bazan iya tashi daga nan ba. ★★★ *M A D E E N A* _ALMUNAWWARA_ *_InterContinental Dar Al Iman Madinah(presidential suit)_* Cikin lallausar jubah yake sanye wadda aka samar da ita da zare da auduga me darajan gaske. Fara ce tas me wani irin daukan idanu saboda tsadajajjen silk material me asalin tsada da aka maida audugar zuwa ga saqarsa. Yana tsaye bakin babban glass window din,wanda kai tsaye idanunsa suke kafe akan haram na masallacin ma'aiki S A W. Tunda suka zo baya gajiya da tsaiwa a gurin......baya gajiya da kallon gurin da yake fata ruhinsa da gangar jikinsa watarana su dawwama a gurin. Koda zai mutu kuma ya zamana yana da rabon qasarsa ta kasance cikin garin me tsarki. Links na jubah dinsa yake sakawa a nutse yana sake qarewa haram din kallo. Yammaci ne sosai,wanda duka duka zuwa sallar magariba bazai haura awa biyu da rabi zuwa uku ba,a awannin kuma yakeso su qarasa ziyararsu saboda kwanaki biyu kawai ya rage su wuce Ethiopia. Wani haske me laushi ke gilmawa ta haram din,tunda yake bai taba ganin garin dake da wani irin shuru me dadin sauraro ba irin madeena,duk da tarin baqi maziyarta ma'aiki S A W da kullum suke cikinsa. Ya kammala sanya links din,ya dafe hannuwansa jikin glass din yana sauke wata ajiyar zuciya me nauyi,ajiyar zuciyar dake tafe da wata irin nutsuwa daga ruhinsa har zuwa gangar jikinsa. Bayan tsaiwar da tayi na kusan mintuna biyar bakin qofar bedroom dinnata tana shaqar daddadan qamshinsa cikin fargabar yadda yau zasuyi face to face bayan wannan damar datayanke masa. Tun a makka tun ranar data dawo daga gurin falaak takejin wani irin tsoronsa yana shigarta. Gani take ko yaya suka kebe zai iyayi mata wani abu,saita maida duk wani ziyara da zasuje ko ibada lallai saita jajibo falaak da maleek,haka suka dinga tafiyar bibbiyu bibbiyu. Ta kuma zabi lokutan dawowarta daidai sanda yake haram ko ya kwanta bacci,kwanaki kadan sukaga juna ita dashi har suka taho madeena. Ko a yanzun wani dan qaramin ciwon kai takeji da mura da tasan bata rasa nasaba da yawan zamzam me sanyi data dinga sha ba adadi. Kwarjini yake mata sosai bayan wannan tsoron,kwarjinin daya sake daduwa tun bayan guraren da suka ziyarta. Gurare ne da tunda take zuwa saudiyya bata taba sanin akwaisu ba ballanta taje. Gurare na tarihi sosai daya shafi annabi Muhammad S A W da sahabbansa. Ba ziyarar kawai ba.....wani abu qwaya daya daya dinga narkar mata da zuciya.....wani abu guda daya daya tilastata ta dinga satar kallonsa har batasan adadin awannin data dauka ba.....wani abu qwaya daya daya sanyata zubewa lips dinsa idanunta tana kallon yadda yake motsa bakinsa,abinda ya dinga tayar mata da tsigar jiki shine. Duk wani guri da zasuje a tausashe da muryar nan tasa da sau tari idan ta kwanta take jinta cikin kanta.....cikin mafarkinta dama duk wani motsinsa.....da wannan muryar yake basu tarihin kowanne guri idan suka tsaya a gurin,da abubuwan da suka afku a gurin zamanin annabi Mohammad S A W. Idan akwai ayar data sauka zai karantata da kyakkyawan sauti da kuma daddadar qira'ar nan tasa. Bata manta ba.....qira'ar ta sanya mutane da yawa waiwayowa suna dubansa,sannan ta qara yawan mutanen da suka bi tawagarsu,dole ya koma bayani da harshe biyu English da arabic saboda mutanen dake biye dasu. Sai kuma taji wani abu yana matse qirjinta sanda taga 'yammata na sake qaruwa,suna biye dasu har xuwa sanda suka kammala ziyaran. Ko a shekaran jiya sunje mazr'a Al'Aaliyah inda nana mariyatul kibdiyya ta haifi sayyadina ibraheem dan manzan Allah S A w. Sunje Daar almadeena museum.... Acan din taga abubuwa masu yawa da aka surantasu cikin killataccen glass da suka shafi ma'aiki matansa da sahabbansa. Gurare ne da suka dinga saukar da wani sanyi da taushi a zuciyarta. Ashe a baya suna zuwa ne kawai ibada ba tare da sun qarawa ibadar armashi ba?. Bata taba umara irin wannan ba a rayuwarta,bata da tabbacin ibadarta,amma zata iya cewa wannan ce umararta ta farko data karbu dari bisa dari. Da wani irin yanayi take takowa zuwa living room din,kamar wata qasaitaccen dawisu. Yanayinta haka me sanyi a wasu lokuta,takun tafiyarta da izza da nutsuwa suka yiwa ado,wannan yana sanyawa idan yana tafiya take jan hakalin mutane sosai,bawai maza kawai ba,harda mata 'yan uwanta. (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) Abaya ce me sulbi a jikinta midnight blue,asalin silk blend me wani irin yauqi da daukan hankali. Wani irin zaunannen kyau tayi,color na rigar yayi masifar fita da kalan fatarta. Dan Malaysian hijabs da ya zame mata abokin sawa tun zuwansu qasar ya fidda kyan fuskarta tare da qara bayyanar da quruciyarta. Ko a yanzun da yake tsaye,motsinta yaja hankalinsa,motsin daya sanyashi waiwayowa a nutse. Wadannan narkkakkun idanun nasa suka sauka saman fuskarta,sai wani abu ya haska cikin idanunsa. Quruciya.....qananun shekarun nan da yayi masifar rainasu,a yanzun yana sake ganin qarancinsu qwarai da gaske. Can qasan zuciyarsa ya samu kansa da irge hasashe da laluben ainihin shekarunta. Ya lumshe idanunsa kadan yana budesu a kan fuskarta,yanayin kallon daya qara mata fargaba ya kuma aza mata nauyi me yawa,sai tayi qoqarin kauda kanta kadan tana nufar inda ta ajiye wayarta dazun bayan shigowarta. "Barka da warhaka" Ta fada da wannan muryartata me wani irin taushi,wadda ko sau nawa zata buda baki tayi magana sai yaji wani abu daban da baisan meye ba a cikin muryar. Maimakon ya amsata,sai ya gyara tsaiwarsa sosai,ya zube hannuwansa cikin aljihun jubah dinsa yana qare mata kallon dashi kansa baisan dalili ba. Yadda fararen qafafunta ke sauka saman tattausan carpet din kamar me tausayin qasa......yadda abayar ke budewa sosai ta bayanta tana bada wasu kaloli kaman ba kalar midnight blue ne kawai a jikinta ba......a hankali duka yanayin suka hadu suka saukar masa da wata irin nannauyan kasala. Yana karance da duk wani takunta tun daga wancan ranar.....wani lokaci siririn murmushi kawai yakeyi. Idan da yaso.....idan da yaga dama ba zata kawo wannan gurin ba. Idan da wani abu daban yake buqata daga gurinta yasan duk ta hanyar da zai karba,bazai ma bata daman da zata iya guduwa daga gareshi ba,to amma ba wannan lissafin yakeyi ba a yanxu. Yana buqatar ta gama sanin wacece ita?,wacce rayuwa tayi a baya?,wacce kalar rayuwa kuma zatayi a yanzu?. Yanaso kuma yaga iya gudun ruwanta gurin qwarewarta wajen guduwa. (Hmmmm Captain.....wata qaddarar tana bada zabi ne?). Har ta qarasa gurin,ta zare wayarta daga charge tana jin nauyin dukka idanunsa a kanta. A hankali takejin wani kusanci a tsakaninsu.....cikin jikinta takejin tabbas yana kusantowa gareta. Ta basar ta danne tana mazewa gami da zarcewa da danna wayarta,duk da yadda zuciyarta ke wani irin bugawa a hargitse,tana kuma bata shawarar ta daga qafarta zuwa waje ya sameta a can,amma ta kasa koda motsin kirki. Ba kasafai ta fiya son a gane lagonta ko faduwarta ba. Batason a gane meye rauninta shi yasa take iya iyawarta ta boye masa tsoronta,saidai abinda bata sani ba.......tana auren wani mutum ne na daban......wani mutum da yake iya karantarka ta cikin qwayar idanunka kadai ba tare daka furta masa komai ba. Motsinka kadai ya isheshi amsa.....motsi kawai wata fassara take bashi me tarin ma'anoni. Jinsa dab da ita da wannan sassanyan qamshin nasa da kowacce rana idan zata jishi sake dilmiyata yakeyi cikin wani yanayi me wahalar fassara. Ta daga fuskarta da sauri,saidai irin kusancin da ta gani a tsakaninsu yafi firgitata sama da komai. Taku daya tak tayi da nufin janyewa baya amma sai ya saka dogon hannunsa ya riqo tsintsiyar hannunta da kyau,bai kuma bata dama kota second daya ba ya janyota jikinsa,saidai kuma bai bari ta fada faffadan qirjinsa ba ya tareta ya tsaidata dab dashi yana riqe qugunta da dukka hannayensa biyun. Kallon kallo suka fara yiwa junansu,nata idanun cike da tsoronsa da wani irin shakka.......zuciyarta na bugawa da gudun da ta sani tabbas idan shuru ya sake wanzuwa tsakaninsu zai iya jin qarar bugun.......yayin da nasa idanun ke cike da wani abu dashi kansa baisan meye ba. Wani abu da yake zama kamar wani dan aike daga idanunsa zuwa na akhnan din.....wani abu da ya yiwa zuciya da qirjin akhnan nauyin gaske.....wani abu daya fara ratsata tun daga qwayar idanunsa yana bin kowacce hanya da jini yake iya wucewa yana sauka kai tsaye a zuciyarta. KAIFI......wani irin kaifi idanunsa ke dashi.....bata taba ganin d'a namiji da yake zarra irin tasa ba. Ba wani namiji data taba kafewa da idanu irin haka bai rusunar da nasa idanun ba.....amma shifa?. Ko yaushe qwayar idanunsu suka gauraya qoqari yake ya dakushe tata. Qoqari yake ya kashe duk wani kwarjini nata ya mamayeta da nasa. *zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 08187255862 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 08187255862 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 37* "Kina zaton idan naso kamaki kina da wani sauran dabaran guduwa ne a hannuna princess akhnan?" Yayi maganar da wani coolness daya daki zuciyarta. Halittar BURGEWA taji tana kafa sansani cikin ruhinta. Burgewa......yadda yayi maganan ya wani burgeta,ya wafci idanu da hankalinta,har ya sanya zuciyarta ta wani irin motsawa da kalar qarfin daya sanyata taji kamar iska dake dakin ta mata kadan,ko kuma shi ya zuqeta tas. Idonta ta kalmashe kawai tana sauraren kalmominsa dake fita a jejjere da wani irin isa da izza. "Kin gama wasan buyan?.....ko na qara miki lokaci biftu?" Ya sake kiran sunanta a qarshe da wani yanayin data tabbatar inda qwayoyin idanunta a bude suke......tabbas da ya gama cutarta......inda qwayoyin idanunta a bude suke........tabbas......ba iya zuciyarta kadai ba.....zai iya karanta rayuwarta ta baya ma gaba daya. "Ki sassauta........bana nufin abinda ke kike tunani" Ya fada yana sassauta riqon da yayi mata. Wani dummm taji....kalamansa na qarshe daya kamata taji farinciki.....kalmarsa ta qarshe daya kamata ta faranta mata rai.......amma saitaji batayi mata ba. Abinda take gudu don shi.......a fakaice ya gaya mata baya gabansa kenan?. Batasan me ya sanyata dora hannunta saman nasa hannun dake qugunta ba,ta kuwa xameshi a hankali don ya sassauta riqon da yake mata din. "Abinda kake tunani ba shine a raina ba.....ai ibada mukazo yi.....ita sultane yace muyi...." Sake matse qugunta yayi fiye da dazu,har tana jin yatsunsa sosai cikin fatar cikinta. Ya sassauta wannan tsahon nasa yana sunkuyowa daidai bakinta,abinda ya bata wata babbar dama na qarewa idanunsa kallo fiye da kullum. Idanun nan dake dauke da wadattatun eye lashes,farare qal kamar ba idanun namiji ba. "Ibada?......ai ibadar ma nau'i nau'i ce......ba umra bace kawai ibada......shima wancan abun ibadar ne". Kamar ya kada mata sassanyar iska cikin hunturu haka matsananciyar kunya ta sanya ta fara ji cikin jikinta. Neman inda zata cure ta cukuikuye takeyi amma babu,sai jikinsa kawai dake tsaye a gabanta. Yanzun me ya kawo wannan maganar fisabilillahi?. Shima haka yake?,shima d'aya yake da sauran?. "Kina tsoro?........bai kamata ki dinga tsoro kan abinda yake da nisan tazara tsakaninki dashi ba" Ya fada yana zare yatsunsa daga qugunta a hankali. "Idan naso......numfashinki me zai zama ba naki bane......a duk sanda zai fita daga qirjinki zai fita ne yana ambaton sunan muhammad haisam......zan sace baccinki......zan gudu da nutsuwarki.......tunaninki gaba daya zan mallakeshi.......ta yadda zaki zama baki da wani sauran xabi.....bakya gane komai sai abinda haisam ya shirya ya kuma tsara miki". Wani irin ego nata ya motsa......wanda yake cakude da tsoro. Anya batayi wani abu na ba daidai ba kuwa da yasa yake ganin yana da dukkan wadannan damarmakin. "Allah ya sawwaqe" Ta fada da wata karyayyar murya. Batason yasan me take struggling dashi.....bata shirya bashi kowacce qofa ba.....saboda bai dace ya fara fitowa daga sashenta ba......bai kamata ace daga bangarenta bane komai ya fara. "Allah ya sawwaqe?,really?" Ya fada fuskarsa tana fadada da wani abu da yafi kama da murmushi,ya dage dukka girarsa sama da alama yanason samun amsa ta gaskiya. "Eh......Allah ya tsareni......har yanzu......ba wani namiji daya cika wadannan sharuddan da qa'idojin" Wani sassanyan murmushi daya sanya har fararen haqoransa a jere reras ya saki,ya sake taku biyar baya yana bada tazara a tsakaninsu,idanunsa kuma still cikin nata,ya riqe qugunsa da hannayensa gaba daya kamar me nazarin wani abu daga gareta. "Au.....eh fa.....na manta wannan din me tsada ce,princess of agadez.....bai kamata almajiiri irina yayi tunanin samun komai haka da sauqi bafa ko?" Ya qarashe da sigar tambaya. "Basai ka yaudarar dani ba bayan yaudarar da sultane da kayi......na sani.....wanda yake magana kamar yana da ikon mallakar zuciya da numfashin mutum… ba almajiri bane.” samun kansa yayi da harde hannayensa a qirjinsa da wani kalar murmushi dashi kansa yasan yakan jima adane a fuska da qirjinsa kafin irinsa ya fita. Sai abu na matuqar burgeshi da daukan hankalinsa tukunna. "Amma kuma......idan kana ganin zaka mallaki tunanina......to har yanzu baka sanni ba tukunna. Don kana magana ne kamar wanda ya riga ya samu nasara......amma kuma har yanzu ban baka wannan damar ba" Wannan karon murmushinsa yafi na dazu fadada. Ya zare hannunsa yana tafashi a hankali. "Bravo princess......." Ya fada da murmushin nan akan fuskarsa. "Shi yasa kika dinga bincike a kaina a boye?" Ya dan matsa gabanta kadan "Kina tunanin na yaudareki harda sultane?" Ya sakeyin shuru na second biyu. "Kinason sanin wanene ni?...." Ya qara fada da wani softness cikin sound dinsa. "Da gaske?" Ya mata tambayar kaman da gaske amsarta yakeson ji,sai kuma ya dora yana maida mode dinsa na farko,miskilanci da izza "Ki kula da abinda kike bincike sosai a kai".... Wannan karon tsoron dake ranta ya ninka wanda takeji a kansa a baya. " Ta yaya?,ta yaya ya sani?,ta yaya yasan ta fara bincike a kansa?,saidai izzarta ba zata bari yaci nasara a kanta ba. "Bincike?" Ta fada tana jan numfashi a boye,saidai duk yadda takai ga boyewar ya ji kaman yadda yake da kaifin jin abu komai qanqantarsa. "Ba kowanne abu bane ake kira bincike....." Ta furta da confidence tana qoqarin kaucewa haduwar idanunsu. "Wani lokaci mutum yana qoqarin fahimtar abinda yake gabansa ne kawai......idan hakan ya sanyaka kaji kamar ana leqenka....." Saita dan dakata tana tattara courage dinta. "To wataqila akwai abinda kake boyewa fiye da yadda kakeso a gani". (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) "Wow" Wani bangare na zuciyarsa ya amsa a nutse ba tare daya furta ba da dukkan qarfin da suka amsa cikin bangwayen zuciyarsa. Tsakiyar idanunta kawai yake kalla. Wannan qwarin gwiwar......wannan zarrar......wannan tsaiwar kafiya da taurin kan......dukkansu.....dukkansu wasu abubuwa ne daya karanta tattare da ita,wasu halaye da yaji sunyi masa. Taurin kai.....zarra kafiya da tsaiwa kan ra'ayi.....ba'a samunsa tattare da lusarin mutum da baisan yau dinsa ba ballantana gobensa. Wasu alamomi ne dake nuna CIKAR MUTUM na sani da ikon zabar meye ya dace dashi. "Okay.....na baki daman ci gaba da bincikata....saidai na miki alqawari........ina miki albishir ba zaki samo komai tattare da wannan muhammad din ba.....kince Allah ya sawwaqe ko?" Yayi maganan duka lokaci daya. "Let's play a game mana......ni dake.....duk wanda yayi winning........i mean,duk wanda yayi nasarar hana dan uwansa satar zuciyarsa......ko ni nayi nasarar saceta.... Akwai wata sadaukarwa da daya zaiwa daya,zai.bashi abinda bai taba tsammani ba....agreed?" Cikin jikinta takejin kamar akwai wani abu daban.....kamar akwai wani abu da bazata iya daukarsa ba..... "Ni ban iya satar zuciya ba.....amma nasan yadda zan kare tawa" Ta furta ba tare data shiryawa fadin hakan ba. Dariya ce taso qwace masa saboda yadda tayin......dariyar daya manta rabonsa da yayita,saidai wannan ginshirar da izzar ta danneta ta maidata qasaitaccen murmushi. "Kina tsoro ne?" "Ni.....tsoro?....." "Yes.....kada ayi nasara a kanki". "Ba'a nasara a kaina....koda yaushe nice nake nasara a rayuwata" "Har a hippodrome?" Ya jefa mata tambayar a bazata,ta kuma sauka a kunnuwanta a bazata din data tilastata waigowa da wani irin zafin nama. Fes idanunta suka samu kyakkyawan matsugunni cikin nasa. Idanun da suka soma narke mata a hankali.....a hankali suna dawo mata da komai yadda ya faru. A wancan ranar.....a wancan lokacin. "Boyayyen mutumin Niamey?,hippodrome?" Labbanta suka motsa a hankali ta furta da wani irin low tone. Zare nasa idanun yayi a hankali,sasaauqan murmushi yake saki,bai kuma bata amsa ba ya fara takawa a hankali yana zura tattausan takalminsa cikin qafafunsa. Takalmin da yayi wani kyau yayi ladabi sosai cikin qafarsa....asalin takalmin gidajen sarauta na oromo. "Game started" Kawai ya fada a hankali yana nufar qofa. Har yakai qofa bata motsa ba,sai daya bude ya sanya qafafunsa a waje sannan yace "Dates farm zamu in sha Allah" Maganan ya bata qaimin data iya cira qafafunta da qyar. Range Rover Autobiography ita ga ya nufa a nutse. Ba yadda ya doshi motar kai tsaye kawai ba.....asalin tsada da darajar motar......yadda ya buda motar da muqullin dake hannunsa kai tsaye ya sake d'aureta kaman yadda ya saba. Ya taka a hankali ya zagaya seat me zaman banza,ya bude mata murfin. Kallonsa tayi kadan,har yanzu kokwanto a kansa yana sake nuqurqusar zuciyarta,amma saita dake ta taka tana shiga motar. Hannunsa ya saka ya tattare mata rigarta cikin nutsuwa,sannan ya rufe murfin motar softly. Yadda yake zagayawa ta gaban motar zuwa nasa seat din cikin karsashi da wani irin kuzari yaja hankalinta. Da idanu ta bishi,maganganunsa suna dawo mata. "Yana da zarra.....yana da zarra irin ta isashen namiji" Ta gayawa kanta da kanta tana lumshe idanunta a hankali. Tako ta ina nema yake ya qure mata,salon iya maganarshi daban ne,kaman sai ya zabi kalmomi yake amfani dasu,kamar kuma yana da iyakacin kalmomin da dasu kadai yake amfani idan zaiyi magana. Qamshinsa ya mamayeta,kusancin dake tsakaninsu ya mata girma,mamakin kuma yadda zai tuqasu da kanshi ya sanyata kasa motsi. "Bismillah" Ya fada yana qoqarin tayar da motar. Kasa jurewa tayi jin ya kunna motar,cikin tsoro takai hannunta saman nasa ta riqe sosai. A nutse yadan daga idanunsa yana dubanta,idon nata ya masa wani irin kala da wani irin haske sanda ta juyashi tana dorashi saman dashboard din motar,tsoro fal cike da blue eyes dinnan nata. "Ka tsaya!" Ta fada adan rude da muryarta data fara rawa. "Me ya faru?" Yayi tambayar a nutse ba tare daya zame hannunsa daga cikin nata ba,saidai ya taka motar da kyau ta fara gangarawa da wani kyakkyawan tuqi. Zuciyarta tadan tsaya cak,ta soma bin gabanta da kallon,yadda yake sarrafa steering cikin wani irin qwarewa kadai ya isa ya bata amsar abinda take kokwanto. A kunyace ta zame hannunta daga cikin nasa,ta danyi qasa da kanta,yadda yayi shuru yana saurarenta nauyi yake sake mata akai,saita yanke kawai kawo qarshen shurun. *zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 08187255862 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 08187255862 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 38* "Na tsorata ne,ban dauka ka iya tuqi ba" Maganan ya sanya murmushi me yawan saman fuskarsa,wannan karon har ya gaza boyewa "Kina rainani ne?" Tambayar ta sake sakata jin kunya,sai kawai tayi kamar bata jishi ba. "Yana da kyau ki koyi tambaya kafin ki yanke hukunci" Ya fada calmly. Har cikin ranta taji maganansa yana kan gaskiya,to amma ta yaya zata iya controlling kanta da dukka wadannan baqin abubuwan da take gani tattare dashi?,ta yaya zata aminta dashi?,ya zata bari ta yarda dashi?. Tana yarda su kasance a muhalli daya ne kawai don suna amintaccen gurin da babu cutarwa a cikinsa. Amma bayan nan gurin.....wannan gurbin....wannan muhallin.....zata sanya idanu da lura sosai a kansa......zata taqaita wanzuwa dashi a muhalli daya har sai ta gano anihi da gaskiyar WAYE SHI?. Shuru motar ta sakeyi,shurun da sam baiyi mata dadi ba. Kaman yasan me yake kai kawo cikin zuciyarta,sai yasa hannu yana daidaita iskan Ac din dake motar. Wani abu data lura dashi,kwata kwata shi ba ma'abocin son sanyin Ac da yawa bane. "Salman alfarisy......wani babban sahabin annabi ne S A W,asalinsa mutumin farisa ne wato iran a yanzu,Ya yi tafiya mai tsawo yana neman gaskiya (addinin musulunci) Ya yi bincike daga addinai daban-daban har ya kai ga Musulunci. Gonar dabino ta salman alfaris,wani tarihi ya nuna annabi ya shuka dabino 300 ne a gurin dukka saboda sakawa salman alfarisi fansar kansa da ubangidansa yayi,akan saiya shuka dabino 300 kowanne ya fito ya bada 'ya'ya anci,yayi hakanne don baiyi niyyar 'yantashi ba,saboda kowanne dabino a qa'ida yana daukan shekara bakwai ko takwas kafin ya bada 'ya'yan da za'aci zuwa goma. Da yakaiwa annabi S AW kukansa,suka hadu shi da sahabbai kowanne da irin dabino,annabi S A W ya dinga karba yana dasawa,sai daya dasa 300 cif,suka kama cikin qaramin lokaci suka kuma bada 'ya'ya kaman yadda ubangidan ya buqata.....da haka salman alfaris ya samu 'yancinsa cikin gajeran lokaci. Amma wasu bangare na tarihi sunce ba haka bane.....amma koma dai yaya ne.....dabino abune me daraja a gurin annabi S A W,zamu so dabino,zamuci gaba da ci,muna fatan samun ladan koyi da sunnah na fiyayyen halitta S A W" Suka qarasa masa salati tare. Kai take juyawa a hankali,tana jin dadin tarihin sosai. Wata dabi'a data fara shigarta,har ta siya litattafai da dama na tarihin sahabbai tsakanin makka da madeena,tana son kuma ta samu dama ta karancesu gaba daya da kanta. A hankali yaci gaba da bata tarihin salman alfarisy,jarumtarsa....hikimarsa gwagwarmayarsa da yaqunan da akayi dashi. Shuru kawai tayi,kanta saman cinyarta,wani irin shuru me cike da nutsuwa,muryarsa kawai take tashi da wani irin laushi da sanyi. Yana fadin komai da cikakken details.....kwanan wata da shekarar da komai ya faru. Sunayen sahabban da suke gurin da sauran abubuwan da suka wakana bayan da kafin sannan tamkar yana gurin a lokacin. Sanda ya fara lissafa mata falalar da madeena ke dashi sai da taji tsigar jikinta tana tashi. Da gaske sunan umara da hajj kuwa take zuwa.....da gaske batasan komai akan guraren ba. Zuciyarta tayi wani irin laushi,hawaye sosai suka cika mata idanunta,qaunar gurin tana sake kamata da gaske,inama tun zuwan da take tasan duk da wadannan falalar da sauran gurare masu daraja haka. (Ya Allah,dukkan musulmin dake da burin zuwa gurin nan don isar wanda ke kwance a gurin muhammad S A W Allah ya qaddara zuwansa......masu niyya da son komawa Allah ya cika mana burikanmu gaba daya,Allah kasa miyita zuwa,ka qaddara shahadarmu acan son hasken fuskar masoyinka muhammad S A W🙏🏽🙏🏽). Batasan sun isa gurin ba,sai da taji motar na magana da yanayin isowarsu gurin,ya kashe motar a hankali,ya waiwaya yana dubanta. Zare seatbelt dinsa yayi,ya ya bude motar ya sauka ya zagaya ya bude mata. Ta jima fuskarta a kife tana qoqarin daidaita hawayenta,yana tsaye harde da hannuwansa kawai yana kallonta,baice mata komai ba har sai data debi adadin mintunan da sukayi mata sannan ta gyara hijab dinta,ta daga kanta idanunsu suka hadu guri daya,saita dauke dubanta a kanshi da sauri. Wani kyau blue eyes dinta yayi masa,wani kyau daya sanya tsigar jikinsa wani irin zubawa harsai daya dunqule hannunsa,yadan cije lips dinsa na qasa kadan,yayi taku biyu baya yana bata daman fitowa. Tun daga farkon gurin tasan gurine bana wasa ba,gurine cike da wata ni'ima da qananun qoramu,wanda iyasu kadai sun isa sanyaya ran mutum. A hankali zuciyarta ta dinga haske tana washewa,ta dinga taka gurin tana ganun nau'in dabinai kala daban daban,wanda tunda take bata taba ganin kalar wani ba. Kowanne kuma da sunansa da launinsa. Dandano ne ta kasa sawa a bakinta,sai taji kaman zai kalleta,zai kalle mata baki yaga yadda take tauna. Tsaiwa kawai tayi tana kallon yadda ake loda dabino cikin boot na motar,idanunta sunyi laushi kaman yadda takejin jikinta gaba daya yayi laushi. Kanta ke mata ciwo tana jin kuma yadda zazzabin jikinta yake sake daduwa,amma kuma ba zata iya gaya masa ba. A hankali ta sake curewa guri daya tana jin sanyin Ac din motar kamar yana son mata yawa,duk da tasani bai saka sanyin da zai dameta har haka ba. Idanunsa akan kyawawan titunan madeena,amma haka kawai hankalinsa yake jin yana kanta. Shurun yayi yawa,ba irin shirun dazu bane wannan. Ya juya a hankali ya zuba mata idanunsa kadan sannan ya janyesu,hannunsa ya miqa kan Ac din motar ya kasheta gaba daya. Zaman da tayi yafi masa kama dana wanda yakejin sanyi. "Kina lafiya?" Ya fada sanda ta taka a hankali zata shige dakinta. Kadan ta waiwaya ta kalleshi,sai ta daga masa kai a nutse ta tura qofar tana wucewa. Minti kusan daya yana tsaye kafin ya janye idanunsa yana duba lokaci. Already sunyi sallar isha'i a can,yau kam jikinsa hutu yake buqata,don ya samu energy na shiga Ethiopia jibi. Ya sake ninkawa kansa nisantar masaukinsu ne saboda ita. Tun daga wancan ranar da abun ya faru.....tun daga wancan lokacin sai abun ya zame masa kamar wani jarrabi. Zai wahala ya kwnata barci bai ganshi cikin wani irin yanayi ba ita dashi. Zai wahala yayi bacci biyar guda hudu bai farka cikin buqatar wankan tsarki ba. Ya tabbatar ci gaba da mu'amalarsa kusa da ita sosai.....zuciya ce bata da qashi,komai zai iya wakana,amma a yau yadda ya gaji sosai,yana saka rai zai kwanta ne yayi bacci me dadi da bazata zame masa barazana cikin mafarkinsa ba. _hmmmm.....anya kuwa?,yau daikam Allah yasa a tsaya iya mafarkin ma_ Ruwa me dumi sosai ya cika bathtub dashi,ya zare kayansa cikin kasala da gajiya ya shige ciki yayi luf abinsa yana jin yadda dumin ruwan ke ratsa qasusuwansa. Kusan mintuna talatin da biyar ya bata sannan ya wanke jikinsa ya fito. Sosai sumar kansa ya kwanta saboda ruwan data nada,hakanan duk wata gargasa dake a jikinsa qirjinsa da hannuwansa,ya daura towel sannan ya dauki qaramin yana rage damshin dake saman kansa. Kaman jira ake ya fito kira ya shigo wayarsa,koda ya duba sai yaga omar ne. "Ya salam" Ya fada yana murmushi,omar ne ya sani,bazai kirashi haka siddan ba sai ya matsanta masa,tabbas sai ya takura masa hankalisa zai kwanta. Baya raba dayan biyun kuma sai da suka gama magana da maleek sannan ya kirashi. "Ya akayi?" Yace da omar yana daga wayar. Wata dariya omar ya saki. Baqon abune a gurin haisam din ya daga wayarka bai fara maka da sallama ba. (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) "Captain.....kome zaka fada ka fada........amma tsokana dole ne". " Halan kana da isashen lokaci ne ko?" "Ko babu zan qirqirar maka". "Alright.....bismillah" Ya fadi yana jan stool ya zauna kawai akai. Ya sani,kafin omar din ya gama iskancin tsokanarsa har jikinsa ma qila ya bushe,don haka bai damu da neman handrayer da zai busar da sumarsa ba,sai kawai yaja body cream da perfume lotion da suke sake sanya gargasarsa ajiye wani irin fitinannen qamshi ya soma shafawa yana jin omar yana duk kalar shaqiyancin da yaga dama. Da qyar ta zare kayan jikinta ta maida gurbinsu da wata tattausar sleeping dress data tsaya iya gwiwa data zo ta tarar birra ta aje mata. Tun da yamman ta sallami birra din bayan birra ta gama komai da tasan zata iya nema a daren,don daman tasan zasu iya kaiwa dare. Saman lallausan gadon da nannade wanda yasha shimfidar offwhite din comforter bedsheet da duvet dukka kala daya. Sannu a hankali zazzabin dake jikinta ya fara yawa,ta soma jin zafin ita kanta a karan kanta wanda yake tafe da wani irin ciwon kai. A hankali takejin zafin zazzabin har cikin idanunta da labbanta,ta sake curewa guri guda tana fesar da iska me zafi daga bakinta. "Bappi" Ta fadi a hankali lokacin da ta soma jin jikinta dukka yana mata nauyi,ta lumshe idanunta tana jin wani irin kadaici yana saukar mata. A hankali ta soma jin yanayin nata yana sauyawa,daga zafin zazzabi zuwa wani irin sanyi me ratsa qasusuwa,sanyin da takejin kamar ba cikin comforter take ba,kamar wadda ke kwance a sararin da babu komai face rigar jikinta zallah "Bappi" Ta sake fadi a hankali idanunta suna tara ruwan hawaye. Sosai ta qanqame pillow din tana cusa kanta a tsakiyarsu. Kewar sultane take.....amma sai takejin akwai wani abu daban data rasa.....akwai wani gurbi daban daba na sultane ba.....akwai wani abu daban da take kewa sama da kewar sultane. Idanunta ta lumshe,hoton fuskarsa ya gilma mata,kafin ta iyayin komai kuma sai wata irin mahaukaciyar kewarsa ta lullube ruhi da zuciyarta gaba daya ba tare data bar mata gurbi komai qanqantarsa ba. "Aah" Ta fada tana girgiza kanta duk da nauyin da yayi mata. Batason ta yarda ko ta aminta da abinda zuciyarta keson gaya mata. Ba haka bane.....tanajin wani kusanci ne kawai ya jawo haka wanda zayazo ya wuce. Hankali kwance omar ke bashi dukka bayanai akan kamun mammina. Yayi relaxing sosai yana saurarensa,bayan ya gama ji din kuma ya gyara zamanshi da kyau. "Sati daya.....sati daya nakeso su riqeta a gurinsu.....kafin satin na kammala da issue din company din,inaso komai ya gama fits lokaci daya". "An gama......amma kamar a wayar uwargida za'a samu phone number nata?,ina buqata zan qarasa wancan binciken daka bani" Kai ya jinjina a hankali. "Alright.....ka riqe wayar ina zuwa" A nutse ya miqe yana zare towel din jikinsa bayan ya saka boxers da moroccon jubah fara tas,jikinsa na fidda qamshin cream perfume dinsa me wani irin qamshi laushi da kwantar da zuciya ya soma takawa zuwa qofar fita ba tare daya saks bedroom slippers dinsa ba. Numfashi ta sake ja sosai tana jin kamar yana neman yayi mata kadan,tana kuma sake cusa kanta cikin pillows din,abinda yake qara mata qarancin iskar da take shaqa. Ya tura qofar ya bude a nutse idanunsa na sauka saman gadon dake nuna alamun akwai mutum kwance akai. Haka kawai yaji wani abu ya fusgi hankalinsa,kai tsaye ya soma takawa zuwa saitin gadon bayan ya biya ya qara hasken dakin ta hanyar kunna qwai guda daya. Saidai yana qara taku daya qafarsa ta taka wani abu,sai ya danja baya da sauri tsigar jikinsa na tashi. Brazier dinta ce fara qal yashe a qasa,sai rigar data fita da ita da under wear dinta data suma a wani gefe na daban. Idanunsa ya zare a hankali daga kan bra din,tuna tuna masa da wancan ranar.......tana tuna masa da wancan yanayin,tunin daya sanya tsigar jikinsa zubawa gaba daya,cikin second biyu kwanyarsa ta harba saqo zuwa ga gangar jikinsa. Zuciyarsa ta motsa kadan daga inda take zaune,cikin kokwanton da shakkar maimaituwar faruwar abinda ya faru a wancan ranar yaci gaba da sanyo kai cikin dakin A nutse ya qarasa gaban gadon idanunsa a kanta,yanayin kwanciyarta,a qudundune cikin duvet ko kanta baka iya gani yasa yaji bai gamsu da yanayin ba. Hannu ya miqa a nutse yana qoqarin janyewa gami da kiran sunanta da wani irin yanayin daya ratsa har kwanyarta,kiran daya sanyata jan wani irin dogon numfashi daidai sanda yake yaye duvet din daga fuskarta zuwa saman wuyanta. Ajiye numfashin tayi tana qoqarin sake jan wani. "Subhanallah......me ya sameki?" Ya furta a rude yana haurawa saman gadon da gaggawa fuskarsa da muryarsa duka suna nuna tsananin rudewarsa,saidai hannunsa kadai daya dora saman sassalkar sumarta data warwatsu tsakanin pillows din dake kan gadon dama fuskarta da tayi wani fayau ya bashi amsa. "Ya salaaaaammm" Ya fada da wani irin yanayi yana qarasa haurawa gadon gaba daya tare da qoqarin dagota gaba daya zuwa jikinsa. *zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 08187255862 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 08187255862 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 39* K'oqarin dagota yakeyi amma yanayin zafin da yaji jikinta yayi da rawan sanyin da yaji tana yi ya sanyashi saketa a hankali ya furta "Subhanallah". Zafin kamar yayi yawa sosai,ya sanya hannunsa a hankali yana zame bargon data rufa dashi din gaba daya. Ta maida idanunta tana lumshewa,hawaye yana sauka ta gefan idonta dake rufe. Sanyi takeji.....sanyi takeji sosai,budetan da yayi ya zama kamar wani qara mata sanyin yayi. Matsawa yayi inda ya ajiye wayarsa ya dauka yana budeta. Kai tsaye yayi kira zuwa ga clinic na hotel din. "Ina buqatar wasu magunguna da allurai" Umarnin daya bayar kenan sannan ya ajiye wayar bayan ya bada number dakin. Dawowa yayi ya tsugunna ta gaban gadon saman qafafunsa,ya daidaita kansa saitin nata,ya zube idanunsa a hankali kan baby face din nan nata da tayi ja,jan da zai nuna maka lallai zazzabin da takeji yakai wani mataki. Hannunsa ya daga a nutse ya dora lallausan tafin hannunsa saman goshinta. Sake lumshen idanunta tayi tana jin yadda laushin tafin hannunsa da duminsa yake ratsa kan nata. "Sannu....." Ya fadi da muryar dake nuna kulawa sosai da damuwa a cikin sautinsa. Motsa labbanta tayi da niyyar gaya masa kanta.....kanta yana ciwo sosai,amma saukar tafin hannun nasa saman wuyanta ya kashe bakinta. A hankali zafin dake saman wuyan nata yake ratsa fatar hannunsa yana aike da wani abu zuwa sassan jikinsa,ya sake zame hannun nasa a hankali yana sauke ajiyar zuciya,daidai sanda saqon ya iso daga clinic din. Karba yayi ya dawo,ya ajiye saman bedside drawer idanunshi still a kanta. Kuka take.....kuka take a hankali,kukan da yaji ya masa nauyi,ya taka a nutse ya sake fita zuwa sittingroom. Cikin mintina biyar wannan hidden princes din ya tako zuwa cikin dakin,dauke da tray,wanda samansa cops ne da wani butan shayi me zubin tea flask. A nutse ya ajiyeta a gefan bedside din. Cup daya ya dauka,ya hada tea din dan kadan ya zuba zuma daidai da irin taste dinsa,don baya amfani da sugar kwata kwata,sannan ya matsa gaban gadon,ya koma ya tsugunna gaban gadon yana sauke idanunsa a kanta. "Zaki iya tashi......don Allah" Ya furta da muryar nan tasa dake da wani sanyi da nutsuwa. Idonta ta kulle sosai tana girgiza kanta alamun a'ah. Shuru ya gilma a tsakaninsu na sakanni. "To na taimaka miki ki tashi?" Ya sake fadi yana kwantar da kanshi kamar me neman wata alfarma. Kai ta sake girgizawa. "Pleeeeaaase" Ya sake fada yana hada hannayensa guri daya. Yadda ya danja kalmar ya sanya taji wani abu me sanyi yana narkewa tsakiyar sanyin da jikinta ke bala'in ji,sai tayi shuru ta kasa cewa komai,wannan ya bashi damar miqa mata tattausan tafin hannunsa dake da wani irin haske me kyau. Jirkitattun idanunta ta bude tana kallon tafin hannun nasa. Suna burgeta.....suna burgeta har batasan iyaka ba. Suna saukar mata wani irin yanayi duk sanda zai hadesu cikin nata.....amma a yanzun sai taji kunyar fara dora nata hannun saman nasa. Baya ga haka rigar jikinta......rigar jikinta tayi tsiraici da yawa,amma kuma batasan yadda zata gaya masa ba. Ba bra a jikinta,sannan saman rigar wani irin net aka shimfida red color daya manne da fatarta sosai ya haska gurin matuqa da gaske. Bata gama daidaita tunanin ba taji an dagata cak,abinda ya sake razanata ya sanya kanta ya sara kadan jin yadda yake rabata da gadon da dukka hanuwansa kamar wanda ya dauki takarda. Hannuwansan ta riqe sosai jikinta da bakinta suna rawa,ta rungumesu sosai cikin jikinta. Tanaso tace masa ya sauketa,tanaso tace masa ya barta ta lullube jikinta,tanason ta gaya masa ba wata riga me kauri bace a jikinta amma dukka tsoro ya hanata,ya qarasa gigitata gaba daya sanda taji yana ajiyeta saman kujera gayarta. Daga sanda ta rungume singalalin hannunsa cikin jikinta,daga sannan yaji ta dasa masa wasu boyayyun halittu cikin jikinta ta aike masa da wani irin makami me qarfi daya soma raunata qarfinsa. Ya sani ba cikin saninta bane zata bashi access da gurin har haka......yayi kuma yaqi sosai da idanunsa akan kada ya kalli gurin. Ya samu nasara,don yana sauketa ya koma ya tattaro mata duvet din saman gadon,ya zagaya ta bayanta ya soma dora mata shi daga saman kafadunta yadda zata zama comfortable,saidai ina.....duk yadda yakai ga son kaucewa kallon gurin.......a sanda yake zagayowa gabanta yana qarasa rufe mata jikinta saida idanunsa suka sauka akai. Fatar gurin tayi wani haske sosai ta sanadin redlace din da aka qawata gaban rigar dashi. Kamar wancan ranar......suna tsaye kyam kamar wadanda suke gayyatarsa zuwa garesu. Wani abu ya fusgeshi har jikinsa yayi shaking kadan,ya cije lips dinsa yana qarasa lullubeta. "Calm down......calm down haisam" Yake gayawa kansa da kansa can cikin kwanyarsa. Saidai duo da wannan qwarin gwiwar da yake bawa kansa hakan bai hana kowacce laka ta jikinsa zarewa ba. Da wani irin laushi ya jawo wata kujerar zuwa inda take zaune. Ya zauna dab da ita,saidai kuma kusancin yayi mata yawa don tana iya jin gwiwarsa tana gogar tata a hankali a duk sanda ya motsa. Idanunsa ya lumshe gami da budesu duka a lokaci guda yana qoqarin controlling kansa. Ya dauka iya wancan wajenne kawai.....ya dauka sune kadai abinda keda qarfin karyashi da kuma raunata karsashi da kuzarinsa......sai gashi a yanzu ya gano wani abu na daban. Dogayen zara zaran yatsun hannunta.......sassalkan gashin kanta daya sauka har kusa da mazaunanta,ya kuma yi mata ado daga gaban goshinta har zuwa bayan kunnuwanta da gaban kunnen nata,yabar mata wani saje me kyau. A duk sanda zai kalli fuskarta da tayi wani fayau....da siraran labbanta da suka danyi dry kadan saboda zazzabin sai yaji wani abu yana tsarga masa. "Take it" Ya fada cikin laushi yana miqa mata cup din tea din daya dauko. Wannan blue eyes din nata da sukayi laushi ta zuba masa,sun tara ruwan hawaye sosai. Ita din ba gwanar abinci bace ko lafiya lau ballantana yanzun da bata da lafiya. Idan tana lalura ruwa kawai take iya sha.....ba magani ba abinci. Tana iya tuna yadda hankalin mammina ke tashi a lokacin,tayita zarya a kanta har sai ta tilastata taci wani abun. Kai ta girgiza masa alamun ba zata sha ba. Idanunsa ya zuba mata a hankali yana kafeta da kallonsa,wannan kallon dake iya tilasta maka yin abinda yakeso koda baka shiryawa hakan ba. Wani irin magnet yake fusgarta dashi,wani irin kashe mata sassan jiki dana zuciya idanunsa sukeyi.....bai sani bane?" Ta tambayi kanta tana qoqarin lumshe idanunta ko zata rage tasirinsu,saboda tana jin yadda wani bala'e'en sanyi yake sake ratsata. "Karbi" Ya sake maimaitawa da sigar umarni. Hannunta ta miqa tana karba,yatsunta suka sauka saman nasa,ya lumshe idonsa a hankali yana budesu gami da zubesu akan yatsun nata da jan lalle ya yiwa wani irin kyau kamar dashi aka halicceta. Dan qaramin bakinta yabi da kallo sanda tak sipping tea din a hankali,ya sake zare dubansa yana jin wani irin abu yana yamutsa masa "Ya salam......haisam.....haisam" Ya kira kansa da kansa internally wai ko zaiji wani abu daban ya amsa kiran bashi ba. Dan qaramin abu ya shimfida mata saman duvet din da take lullube dashi don kada ta batashi,saidai ko kurba biyar batayi ba ta sauke cup din tana langabe kai idanunta cikin nasa. Bata tana ciwon da taci abinci haka ba,kuma ko a yanzun tasha yakai har hakanne saboda tsimammun idanunsa daya kafeta dasu. "Ya isa" Lumshe idon ya sakeyi ya budesu duka a lokaci guda da wani irin calmness,ya motsa kyawawan labban nan nasa masu wani irin surkin red da pink. "Ki sake qarawa" Ya fada a hankali kamar bayason yin maganar. Inda wani ne.....inda kuma zata iya zatace masa aah,amma kaifin idanunsa baze bari tace komai ba,ta langabar da kanta,ta sake kurba uku,wannan karon a shagwabe ta fadi. "Ya isa" Saboda yadda taji kamar zai dawo. Dif yayi wani abu yana tsinkewa cikin kansa. Yadda tayi maganar da wata irin narkakkiyar shagwaba saita zama kamar tsokana a wajensa. Bai iya cewa komai ba,ya miqa hannu ta saka masa mug din ya maida saman tray din,sannan ya matsa baya yana jawo ledar da aka kawo daga pharmacy din. *_Assalamu alaikum warahmatullah_* *_Akwai pyjamas/home wear/lounge wear tsala tsala masu dadin zaman gida da bacci_* *_Sabbi kar a mutunce cikin jakarsu,a affordable price_* *NA IYAYE DA YARANSU* *_kina kasuwancinsu?,Maza zoki gwada wadannan dana kawosu......quality dinsu ya girmi farashin_* *_ki siga ki siyawa yara.....masu dadin sawa a zafinnan.....ga taushi ga ba nauyi_* *_maza tuntubi huguma ta nan don ki ganewa idanunki_* 08187255862 Zazzagesu yayi saman gadon yana dubawa. Duk da azababbben sanyin da takeji hakan bai hanata qare masa kallo ba,idanunta can qasa kamar bashi take kalla ba. Komai nasa very calm,ba calmness me tattare da sanyin jiki ba.....aah calmness me cike da kuzari,saidai nutsuwa ta mamayi komai nasa. Tana jin wani tsoro yana mamayeta,tsoron yadda ya sanya take fara jin wani abu me qarfi cikin zuciyarta tattare dashi. Tsoron MEYE WANNAN? Da yake dasuwa a zuciyarta ba tare da shawara ko neman izini ba. Tsoron wani irin feeling.....strong feeling da bata taba jinsa tattare da kowa ba. Nutsuwar nan tasa me cike da izza shine abu na farko da yake sake daukan hankalinta. Tsugunnawar daya koma yayi ya sakata janye idanunta cikin tsoron kada ya ganta,a daidai sannan idonta ya sauka akan allurar daya dauko yana farketa a ledar yana kuma ajiye cannula a gefe. Hantar cikinta ta kada sosai,wani tsoro ya saukar mata a hankali. "Allura" Ta fada a hankali tana jin tsoro yana sake shigarta. A tun tasowarta magani da allura suna cikin manyan abokan gabarta. Magani da allura suna cikin abubuwan da sam bata shiri dasu. Tana iya boye ciwo kawai don kada ace ga magani.....tana iyayin zamanta da ciwo kawai don kada ace za'ayi allura. Tayi rau rau da idanunta sanda ya zauna a gabanta,idanunsa cikin nata,nata kuma yana kan allurar tana sake narke idanun nata,ruwan hawayenta suna sake daduwa. Ji takeyi kaman nata ya qare......har wani qarin sanyi takeji yana sake ratsata. Duba daya yayi ma qwayar idanunta,Karo na farko da yaga raunin wannan princess din. Karon farko da yaga hawaye a idanunta har haka,karon farko da yaga lagonta akan zazzabi da allura. Dogayen yatsunsa ya miqa mata,saita daga idanunta tana kafeshi da kallo a wani mugun tsorace. A wannan lokacin banda yayi da mugun gaske dariya ce tsaf zata kubce masa. Duk tsaurin ran mace da kafiyarta,qanqanin abu kaman allurar sai ya tsorata ya raunatata ya kuma nuna rashin qarfi da wayonta. "Eheennn" Ya fada yana motsa mata yatsunsa alamun ita yake jira ta bada hannun yasa mata cannula. Noqewa tayi tana sake cukuikuyewa cikin duvet din kamar zata bace a cikinsa,sanyi kuma yana sake kadata. "Please" Kawai ta fada da turanci duk da bata shirya magana da harshensa ba. Idanunsa ya kafe mata,sannan a hankali idanunsa suna lumshewa......wani irin kasala yana lullubeshi da kalan shagwabar da yake gani a yau dim tattare da ita. Ta narke gaba daya,kaman ba itace wannan princess din ba,.....me qarfin halin marin d'a namijin daya shiga gonarta duk girmansa da matsayinsa. Wadda ta kada 'yan maza goma sha hudu.....takejin komaima ta tsere masa tafi qarfinsa. "Bakya ganin yanayinki?.....temperature naki is so high......zaki iya shiga level na convulsion fa?" Ya fada yana dage dukka girarsa biyun sama da wani sautin da koda kana cikin dakin ba lallai kaji magananshi. Allurar da cannula din ta sake kalla sannan ta kalleshi. "Kinaso na riqeki ne?" Saita girgiza kanta da sauri hawayen data maqale yana sauka daga idanunta "Am.....amma ka cire wannan" Ta fada da rawar murya tana nuna cannula din. Idanunsa ya janye daga kanta,haka kawai yaji wani irin tausayinta yana ratsashi. Yaso yayi amfani da cannula din saboda allurar tafi saurin bin jininta ta sauke zazzabin,amma tunda haka ta zaba,sai yaji bari ya cire din. *_Assalamu alaikum warahmatullah_* *_Akwai pyjamas/home wear/lounge wear tsala tsala masu dadin zaman gida da bacci_* *_Sabbi kar a mutunce cikin jakarsu,a affordable price_* *NA IYAYE DA YARANSU* *_kina kasuwancinsu?,Maza zoki gwada wadannan dana kawosu......quality dinsu ya girmi farashin_* *_ki siga ki siyawa yara.....masu dadin sawa a zafinnan.....ga taushi ga ba nauyi_* *_maza tuntubi huguma ta nan don ki ganewa idanunki_* 08187255862 *zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 08187255862 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 08187255862 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 40* "Oya.." Ya fada yana sake bata hannunsa. Kaman zata tashi ta zura da gudu haka ta miqa masa hannun,ya riqe tsakiyar tafin hannunsa yana kallon tattausan farar fatar dake shimfide a singalilin hannun nata. "Wayyo bappi....." Ta fada a raunane sanda yaje da allurar dab da fatarta. Tsaiwa yayi cak yana dubanta,ta cure sosai tana rawar sanyi,tausayinta yaji ya sake kamashi a karo na biyu,sai yake jin kaman zaiyi wani abu ba daidai ba,sai yake jin kaman zai taba amanar da aka bashi ne. A hankali ya maida allurar ya ajiye,a can cikin zuciyarta tayi sak tana jiran taji tsinin allurar amma sai taji shuru,a maimakon hakan,sai wannan husky voice din nasa daya mamayi kunnuwanta da haruffan sunanta da taji suna ratsa qasusuwanta. "Aakhnaaan" Sassanyan numfashi taja a boye tana saukeshi,ya sake maimaita kiran nata yana dorawa da "Kallo nan" Bata musa ba.....don bugun da zuciyarta keyi....ya gauraya da kiran sunanta da yayi ya qara mata jin wani irin sanyi. A nutse ya lalubo qwayar idanunta ya saka tashi a ciki,ya sanya babban dan yatsansa a hankali yana murza fatar hannunta. "Ki nutsu....uhnnnn.....bazan miki da zafi ba,kija numfashi sosai ki fitar a hankali.....na miki alqawari,kafin ki gama fitar dashi an kammala.....do you trust me?". A hankali kamar me ciwon wuya ta daga kanta. "Alright.....ci gaba da kallona.....karki dauke idanunki,zan gane idan da gaske kike" Ya fadi yana lumshe idanunsa a nutse sannan ya budesu a kanta. Tana jin sanda allurar ke ratsa fatarta a hankali,saidai wani yanayi ne da bata taba kawowa zata jishi ba. Ba wani abu da takeji na tsoro ko firgici a duk sanda za'a mata allura irin haka,tafijin yadda yake sake mata wasu abubuwa kai tsaye daga manyan fararen idanunsa zuwa nata idanun akan shigar allurar jikinta. "Finished" Ya fada a hankali yana tura kujerarsa baya yana sakin wani numfashi can qasa. A karon farko yaji wani abu na daban.....lokaci na farko daya taba jin wasu idanu suna dauke da wasu abubuwa masu nauyi.... Nauyin da suka dinga ajiye masa wasu abubuwa masu nauyi da kashe jiki. Qasa tayi da idanunta tana jin wata kunya tana kamata. "Daga yin allura?,saiki saki idanu da baki kina kallonsa?.....kamar ma dai......" Da sauri ta katse zuciyarta ta hanyar takurewa gaba daya cikin duvet dinta. "Zaki iya kwanciya don allurar yabi jikinki?,zai iya daukan awa daya zuwa da rabi saboda bana jijiya bane,yana kuma aiki ne a hankali" Ya fada sanda yake tattare kwalaben yana adanawa cikin dust bin. Kai ta gyada masa,sai ya taka a hankali ya sake gyara mata gadon. "Getup" Ya fada a tausashe yana kallonta duk da ta boye dukka fuskarta cikin duvet din. Kai ta girgiza "Zan tashi da kaina....zan iya" Hannunsa dake nade a qirjinsa ya sauke,ya juya ya soma takawa yana barin dakin ba tare da yace da ita komai ba. Haka kawai sai ya gaza nutsuwa bayan ya koma dakin. Sundan qara waya da omar yace masa batajin dadi,ya bari zuwa gobe saisu qarasa aikin. "Allah ya bata lafiya......amma dai a dinga sassautawa farin shigar nan" Bai wani yi nauyin fahimtar abinda omar ke nufi ba,don ba qanqanin yaro bane shi. "Omar.....omar" Ya kira sunansa har sau biyu yana rasa me mai zaice masa. Wannan din ya sanya omar dariya sosai. Ba kasafai haisam ke denying abubuwa ba,idan ka fada yana barinka ne da fahimtarka kawai,amma yau din yadda yake qoqarin cewa wani abu sai ya bashi dariya. "Nidai bance komai ba......asuba ta gari Mr lowering gaze" Shuru haisam din yayi na sakanni kafin ya sauke wayar yana dan qaramin murmushi,jikinsa ya bashi da alama gulmarsa kawai akeyi tsakanin su shidan,amma ko meye zasu hadu a Ethiopia,kowanne a cikinsu ai yasan halinsa. Ya kammala komai ya kwanta,amma haka kawai sai zuciyarsa ta kasa nutsuwa. "Amana ce.....amana ce a hannunka" Wannan kalmar ta sakashi sauke qafafunsa qasa,ya dauki wayarsa ba tare daya damu da sanya slipper dinsa ba ya bude qofar ya fito. Yana tura qofar dakin yaji yunqurin amanta tun daga toilet "Ya salam" Ya fada a rude yana qara hanzarinsa da kuzarinsa ya isketa cikin toilet din. Dafe take da sink amma qafafunta da sukayi laushi saita kasa tsaiwa sosai,ga yunqurin aman dake sake jigatata. Wani irin riqo yayi mata cikin jikinsa yana supporting nata sosai,riqon da yazo mata a sanda take buqatar hakan,sai kawai ta sake sallama tana bar masa daman riqetan da yakeso yayi,aman ma kaman jiransa yakeyi sai gashi ta farar da amayar da tea din dukka da tasha dazun harda guntun dabinon da taci a salman alfarisi date farm. Sosai ta amayar da komai,tanata qoqarin sakarwa aman ruwa don kada ya gani amma sai ya riqe hannayenta gaba daya cikin nasa. Ta daga blue eyes dinta da suka jigata sosai suka hada idanu,sai taji wani nauyinsa yana saukar mata. Yaga qazantarta sosai,ta dauka zataga sauyi ne a fuskarsa,amma sai take hangen wani tausayi shimfide saman kyakkyawar fuskarsa. "Kin kammala ne?" Sadda kanta tayi qasa,a duniya bata dauka akwai wanda zai mata irin yadda sultane yake mata ba. Yana tsaye dab da qazantar amanta amma kuma kulawa kawai da damuwa take gani akan fuskarsa ba qyama ba. "Eh". Ruwa ya dinga zuba mata tana wanke fuskarta da bakinta. Yabi hannuwanta da kallo yadda suke kakkarwa,ta kammala ya jawo qaramin towel ya damqa mata. Ta dauka iyaka kenan,sai taga ya riqe tsintsiyar hannunta,bai kuma saketa ba sai daya tabbatar ta kwanta sosai ya maida duvet din ya rufeta. Idanunta a lumshe numfashinta yana sauka a hankali,tana jin qarar ruwa a toilet din,tana jin alamun wanke sink din dama duk gurin data bata da qaramin brush. Slippers din ya zare daga bakin toilet din,ya tako a nutse har zuwa bakin gadon. Tana jin tsaiwarsa amma ta kasa bude idanunta saboda sanyin dake nuqurqusarta. *_Assalamu alaikum warahmatullah_* *_Akwai pyjamas/home wear/lounge wear tsala tsala masu dadin zaman gida da bacci_* *_Sabbi kar a mutunce cikin jakarsu,a affordable price_* *NA IYAYE DA YARANSU* *_kina kasuwancinsu?,Maza zoki gwada wadannan dana kawosu......quality dinsu ya girmi farashin_* *_ki siga ki siyawa yara.....masu dadin sawa a zafinnan.....ga taushi ga ba nauyi_* *_maza tuntubi huguma ta nan don ki ganewa idanunki_* 08187255862 Idanunsa ya zube fes a kanta,sai ya lura da yadda haqoranta suke haduwa guri daya amma tana qoqarin hana hakan faruwa. Aman da tayi relief ne yasan zata samu.....amma baisan me yasa har yanzu sanyin da takeji yaqi raguwa ba,da alama jininta yana da qarfi sosai. Har qasan ransa yaji bazai iya tafiya ya barta a haka ba,sai ya juya a nutse ya fara bude windows na dakin tunda ba fanka ko Ac,dole su baqaci fresh air komai qanqantarta. Ta cikin rufaffun idanunta take iya ganin duhun daya mamaye dakin. Ta cikin rufaffun idanunta take iya jin motsin haurowarsa gadon,hakanan ta cikin rufaffun idanunta takejin sanda ya janye duvet din,saidai abinda ya bata mamaki lokacin da taji ya hauro daya side din ta samanta,ya kuma fara laluben zip na sleepwear din jikinta. Duk wata tsiga ta jikinsa saida ta zuba saboda wrong position daya dora hannunsa. Maimakon ya kama zip sai hannuwansa suka tafi wani guri na daban. Kamar an jona masa wutar lantarki a jikinsa haka yaji wani irin shock daya harba tare da harbawar jinin da zuciyarsa take aikewa a kowanne second zuwa sassan jikinsa. Abun yazo mata a bazata....wannan ya sanya numfashinta ya dauke na wucin gadi ta kuma kaiwa hannunsa cafka ta riqe sosai zuciyarta na dokawa da matsanancin qarfi. "Ka......kkkaaaaa" Sai kuma ta kasa fada,ta kasa hada haruffan saboda bugun da zuciyarta keyi din ya hana daidaituwar kalaman saman harshenta har sukai ga fita. Yasan me takeson fadi,sai kawai ya sauqaqe mata,ya saukar da kanshi daidai kafadarta,da wani irin sauti da yayi ma kunnuwanta laushi da yawa,sautin da yafi kama da rad'a yace. "I'm.....I'm sorry.....“That wasn’t my intention.” ya fada yana dakatawa kamar wanda ke zaben kalmomin da zaiyi magana dasu "......yi directing dina zuwa zip..........sanyin da kikeji yayi yawa" Ya fada yana jin kalaman kamar zasu qwace daga bakinsa,don abinda yakeji a yanzun cikin jikinsa kamar zai wuce ne da numfashinsa. Duk magananshi da harshen France yana sake sawa komai yana qwace mata ne....muddin zai bude wannan husky voice nashi ya yara mata french to yana sanyata tajita kaman ZERO,yana sanyata tana jin kaman bata iya komai a yaren ba....kaman bata iya pronouncing na yaren yadda ya dace ba....ballantana yanzu. Muryar dayake mata magana dashi wata murya ce ta daban,wata murya ce ba kalar wadda ta saba ji daga gareshi ba. "Nooo..." Ta fadi tana dan jan kalmar da dan tsaho. Akwai kafiya cikin muryarta,shi kuma ba wannan yake buqata ba a yanzu. Koda wanne lokaci zata iya loosing yanayinta inde bai samar mata da abinda zai bata dumi sosai ba.....ba kuma abinda zai wannan aikin nan da nan sai skin to skin. A hasashensa cikin duhun ya sake kai hannunsa jikinta,cikin sa'a ya dora hannunsa akai,saidai akwai alamun nata hannun yana gurin. Ture hannun gefe yayi,ta buda baki da niyyan magana tana son maida hannunta gurin,saidai hannun nata a ainihin fatarta ya sauka don tuni yakai zip din qasa. A nutse ya soma sabule mata rigar daga kafadarta zuwa daya kafadar,dukkanin labbanta rawa suke,magana takeson tayi amma bata da wannan energy din. Wani irin yanayi ne me wahalar fassara a gareshi.....bashi kadai ba,ga duk wani kamammen namiji daya adana samartakarsa hakance zata kasance dashi. Dukka hannuwansa rawa suke lokacin da yayi mata kyakkyawan masauki cikin faffadan qirjinsa,ya maida hannuwansa dukka biyun ya mata kyakkyawar runguma. Fatarsa ta manne da tata,yalwataccen gargasar nan me santsi dake lullube da qirjinsa ta sauka gefan kuncinta......fuskarta ta nutse tana samun kyakkyawan masauki cikin qirjinsa. Karo na farko a rayuwarta da wani d'a namiji ya kusanceta irin haka.....kamar yadda ya zama karo na farko da wata diya mace ta kusanci gangar jikinsa har haka......sannan yaji kaman kusancin yanason kutsawa tare da danna kai ya zarce iya skin nasa kawai. Kamar akwai wani abu dake qoqarin bonding nasu da wani irin zafi da sauri me kama da walqiya. Sake boyeta yayi sosai cikin qirjinsa yana jinsa a hankali yana fita daga ainihin wannan duniyar zuwa wata duniyar ta daban,hancinsa yana zuqo mata daddadan qamshin da lallausar sumarta da fuskarsa ta shige ciki tayi mayafi da ita. numfashin da yake zuqa a yanzu cikin hancinsa yana jin cewa ba ainihin numfashinsa da yake shaqa bane a kowacce rana. Bugun da zuciyarsa takeyi a yanzu yana jin ba ainihin wannan zuciyar bace a qirjinsa a yanzu.....duniyar da yake ciki.....mintunan dama awannin dukkaninsu ba irin sauran awannin da yayi a shekarun rayuwarsa gaba daya bane. *_Assalamu alaikum warahmatullah_* *_Akwai pyjamas/home wear/lounge wear tsala tsala masu dadin zaman gida da bacci_* *_Sabbi kar a mutunce cikin jakarsu,a affordable price_* *NA IYAYE DA YARANSU* *_kina kasuwancinsu?,Maza zoki gwada wadannan dana kawosu......quality dinsu ya girmi farashin_* *_ki siga ki siyawa yara.....masu dadin sawa a zafinnan.....ga taushi ga ba nauyi_* *_maza tuntubi huguma ta nan don ki ganewa idanunki_* 08187255862 *zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 08187255862 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 08187255862 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽 💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 41* Cikin qasa da second biyar taji gaba daya an zare mata sha'awar yunqurin qwatar kanta da takeyi.....cikin qasa da second biyar ta soma jin wani irin mani'imcin dumi yana ratsata.....cikin qasa da second biyar ta soma jin wata irin nutsuwa me aminci tana mamaye gangar jikinta da ruhinta gaba daya. Numfashi taja me nauyin gaske,wanda ya zuqo mata anihin qamshinsa na gasken gaske dake tashi da laushi a gargasar dake qirjinsa wadda tafi kowanne luxury pillow data taba using saboda bacci santsi laushi da wani irin calmness. "Oud Wood,Baccarat Rouge,Amouage Interlude,Midnight Oud,Royal Ember,His Scent" dukka cikin turarukan ta gaza gano wanne ne ainihin turarensa?,wanne irin qamshi ne wannan me azabtar da zuciya?. Qamshinnan nasa… mai ɗumi da laushi… yana manne da shi a dukka wani yanayi na rayuwarsa,dare ko rana,kamar wani bangare na jikinsa,wani abu ne da ba a iya mantawa da shi ko bayan ya tafi. "Zan zauce......please,kaman ina loosing control dina" Ta motsa labbanta tana fada a hankali,saidai ta barwa zuciyarta da fatar bakinta sirrin abinda takeson fada din. Tana jin kamar ta furta,amma wani abu yana danne mata kalmominta. Ta lumshe idanunta tana jin wani yanayi yana fusgarta. "Me nakeji?,ya Allah" Ta fada tana lumshe idanunta,wani irin feeling da bata taba jinsa ba yana taso mata,saidai bata kalleshi da idanun ma'anarsa ba,sai wani abu na daban. Idan yace ya rasa hayyacinsa da ita riqon daya mata kawai na wasu mintuna bazai qaryata ba. Abu daya ya iya ganewa,saukar numfashinta a hankali,da gumin da yake goshinta wanda ya fara ratsa fatar qirjinsa,sai damshin da yaji daga gadon bayanta inda tafukan hannayensa ke kwance a gurin saboda tsaro....gudun qetare iyaka,tabbacin zazzabin da yayi mata mummunan kamu ya sauka kenan. Yayi shuru yana jin yadda jikinta ya sake gaba daya.....yana jin yadda iskar numfashinta ke fita da wani irin nutsuwa. Koda ba'a gaya masa ba ya sani bacci ne ya dauketa,irin baccin nan dake cike da nutsuwa me yawan gaske. Tunda ta fara gumi dole ya rage duvet din da suke ciki,ya yayeshi gefe yana kallon window da yake ganin fatsi fatsin ruwa,daya saurara sosai sai ya fahimci ruwan sama ne yake sauka,wannan ya sanya wani sabon zafin tasowa. Yabi siririn hasken dake shigowa dakin ta tsakanin labulen dakin,wanda ya sauka direct a kafadunta. Ya sauke idanunsa a hankali,mamaki kadan yana kamashi,duk da cikin duhu ne amma hakan bai hanashi ganin glowing skin nata ba. "Hasbunallahu wa ni'imal wakeel" Ya furta yana jin wannan abun daya danne yana taso masa yana kuma nema yafi qarfinsa fiye da dazu. Cikin ransa yakejin inde bai tashi ba.....inde bai canza makwanci ba komai yana iya faruwa. Ya fara rasa control dinsa......ya fara jinsa sama sama......ya fara jin kamar numfashinsa yana neman qwace masa. Ya yunqura sosai zai miqe,daidai sanda akayi wata tsawa data sakata farkawa daga baccin daya mata wani irin dadi. Ba tare data shirya ba ta damqeshi da kyau tana sake qanqame hannuwansa a muhallin da yakejin hadarinsu a tattare dashi yafi hadarin bindiga me bullet. Tun ba yau ba....tun a wancan ranar ya gama karantar tana tsoron tsawa,amma a yanzun kalan riqon data masa bazai harfar musu da d'a me ido ba. So yake ta sakeshi,ta gyara kwanciyarta,ya kunna Ac,ya dawo ya kwanta koda daman sofa bed ne ko saman Normal sofa,don tunda aka fara ruwa yasan shima bazai barta ba,ba zata iya kwana ita daya ba "Sakeni" Ya samu ya furta da qyar,don bayajin zai iya mata dogon jawabin ba tafiya zaiyi ba. "Tsoro nakeji don Allah" Ta fada muryarta na rawa,hankalinta yana kan window din,saboda walqiyar da ake sakeyi ta tabbatar wata tsawar a gaba na nan zuwa,ba kuma tare data lura da muhallin da taketa riqe masa hannu ba. "Ki sakeni mana" Ya sake fadi wannan karon yana dan kausasa muryarsa kadan saboda ya fara loosing control dinsa. "Kark......" Ragowar kalaman dukka basu gama fita ba tsawa ta biyu ta biyo baya,wadda shi kansa ya jita,bai gama fahimtar komai ba kuma ya jita cikin jikinsa da wata irin kalar runguma me tsaurin gaske. Kuka yake qasa qasa,kukan da yake iya jin qananun sautikansa a qirjinsa. Bappi take kira,kamar wata qaramar yarinya,yadda kuma take kukan zai fada maka daga can cikin zuciyarta ne. A gurinta ne sautin yake kuka,amma a gurinsa tamkar sautin gayyata ne take aike masa zuwa wata duniyar ta daban. Yayi duk dabarar da zai qwace amma yadda ta riqeshin ma sake zare masa duk wani karsashi take sakeyi. Tsaiwa yayi cak yana jin yadda kunnuwansa suke nisa da duniyar da yake ciki.....hankalinsa yake dada nisa dashi.....tunaninsa yake sake dauko masa wani yanayi na musamman........kaman yadda duk wani sake shige masa jiki da takeyi yakejin kamar tana tura masa komai da komai ne wanda direct yake isa ga fatarsa. Wani sabon salon skin to skin yakeji tana masa.....wani yanayi me firgita hankalin me hankali,da jirkita nutsuwar me nutsuwa duk kuwa kalan nutsuwar da yake tutiyar ya mallaka. Bashi da wani zabi face bin abinda zuciyarsa take ayyana masa,a hankali ya dora hannuwansa guda daya akan bayanta,daya hannun nasa kuma ya riqe bayan kayanta da kyau,hannuwansa suna nutsewa cikin sassalkar sumarta. Fuskokinsu ya hade guri daya,tsinin hancinsa ya sauka akan nata,sai ya soma gogawa a hankali yana fadin. "Aakhnaaan" Da wani irin rarraunan sauti daya sanya tsigar jikinta tashi. "Na'am" Ta amsa tana qoqarin dauko tunaninta ta dawo dashi gabanta. Sake kiranta yayi,ta sake amsawa,a karo na uku kuma daya sake kiran nata sai kiran ya fito a wani irin zafafe,ya hada kuma da saukar hannunsa saman wancan gurin da ta kawo masa da kanta ba tare data sani ba. A nan duk wani lantarki na jikinta ta tsinke,a nan ne tunaninta da yayi nisa a dazu ya dawo,ya karanta mata cewa suna saman gado daya,bata da riga baida riga.....tunaninta ya sake karanta mata wani irin saqo me wahalar fassara data soma jin yana aike mata,tunaninta ya sake finciko mata saukar hannuwansa a gurare da dama na jikinta,bata kuma sake tuna komai ba sai taji ya game bakunansu guri daya yana aike mata da wani zazzafan kiss kai tsaye baki da baki. (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) Wani irin nauyi yake sauke mata,nauyin dake nuna mutumin daya dade yana riqe kansa. Wani baqon abune da bata taba jin irinsa ba tunda tazo duniya.....wani irin yanayi da bata taba kawoshi zai faru a kanta ba nan kusa. Ya yaye dukkan wani hijabi dake tsakaninsu,ya kai hannunsa dukkan wani sashe da yake cikin alfarmarta da alfaharinta na diya mace,ya ajiye fuskarsa a duk wani guri da takejin yana da tsananin girma da kima da tsaro a gurinta. Ta tureshin ta kirashi da mabanbantan suna amma bataci nasara ba.....daga qarshe kawai abinda ta yanke.....kiran sunan sultane da dukkan muryarta,wani abu daya sanyashi tsaiwa cak.......jikinsa yayi wani irin laushi,ya zame a hankali yana kwantawa a gefe rub da ciki yana runtse idanunsa da kyau,ya cije labbansa na qasa sosai yana jin wannan yanayin yana ratsashi,yana lalube cikin kwanyarsa yadda zai samu relief. Dukkan qarfinta ta sanya tana tattaro duvet din duk da girman da yake dashi tana lullube jikinta gami da curewa guri daya. Wani irin tsoro ne yake ratsata,ta tabbatar banda Allah ya mata ludufi zazzabin ya sauka ba abinda zai hana tsoro ya sanya ta shide gaba daya. Ya damqe bedsheet din sosai cikin hannunsa kaman zai tsagashi,ya sauke wani numfashi a hankali jikinsa yana qarasa saki gaba daya. Sai a sannan sautin kukanta ya soma dawo masa cikin kunne. "Me nayi mata ma?" Ya tambayi kansa yana tuna a daidai gurin data sanya masa iyaka. A gurin daya tabbatar inda ya isa can din da yanxun wani sunan daban zai amsa haka ita dinma. A hankali nutsuwarsa ta dawo jikinsa,yana kuma jin sautinta a hankali,saidai haka kawai yakejin baida energy din da zai iya cewa da ita komai. Ya kusa mintuna talatin sannan ya iya miqewa,har wani jiri yakeji bayan nauyin da jikinsa yayi masa. Ta dauka zai fita ne zuwa dakinsa,amma ga mamakinta sai taga ya wuce zuwa bathroom dinta kai tsaye. Tana jin saukar ruwa daga bathroom din wanda ya tabbatar mata wanka yake. Jin komai take kamar a mafarki,har yanzu a gigice take jinta,ta kasa gasgata abinda ya faru tsakaninsu koda na minti daya. "Inda ya samu nasara fa?" Zuciyarta ta jefa mata tambayar data sake sakata fashewa da kuka. Da tuni shikenan,asirinta zai tonu kenan kamar yadda na falaak ya tonu a idanunta? Tun wancan ranar bata sake bari sun hada ido da falaak ba,haushi haushin falaak din takeji,ita kuma kunyar akhnan takeji. Da sauri ta maida kanta gaba daya ta lullube a duvet din. Haisam ne......daure da towel a qugunsa,yanayin da yayi matuqar gigitata.....yanayin da bata taba zaton zai iya aikatawa ba. Fitowarsa a haka ba riga,duk wani siffar qarfi nashi ya bayyana ta qaramin hasken bedside lamp daya kunna. Wannan lallausar gargasar da takeji kamar tana ajiyar qamshi na musamman......wannan faffadan qirjin,santala santalan hannayensa duka a fili muraran. "Kina buqatar wanka?....akwai ruwa a bathtub fresh" Ya fada da wani yanayi na kulawa a muryarsa. Ba shakka inda akwai daman dan adam ya bace ba abinda zai hanata bacewa. Yana mata magana kanshi tsaye,dab da kanta yadda take iya jin damshin jikinsa ta hannunta daya da bata lullube ba. Wato tambayarta yake a fakaice shin takai inda yakai?,koshi kadai ta raka ta dawo?. Wani kukan kunya ya qwace mata. Ta tabbatar a yanzu jikinta ba inda hannunsa bai kai ba,ba inda hannunsa bai taba ba,shikenan bata da wani sauran martaba da daraja?. Ya akayi ma ta barshi har saman gadonta?,ba'a kansa kadai ba,tasha ganin kallon sha'awa a kanta daga idanun maza masu tarin yawa,wannan dalilin ya sanya ta tsani kallo daga idanun kowanne d'a namiji. Bata taba ganin ya mata wannan kallon ba,shi yasa ta sakankance,bata taba kuma kawo hakan a ranta game dashi ba,ashe zai bata mamaki. Mamakin kuwa yaso bata sanda yake bata zabin taje tayi wanka ko ya dauketa da kansa ya kaita. Hakanan ta tattare duvet din tayi toilet dashi,tanata satar kallonsa,saidai shi idanunsa ma baya kanta,yayi tsaye ne a saitin qofar glass dinnan dake nuna masa Haram na madeena kai tsaye. Sau ba adadi yana lumshe idonsa yana budewa cikin haram din,wata irin tarin nutsuwa yakeji tana saukar masa. Ambaton sunan Allah kawai yake cikin ransa yana motsa labbansa kuma a hankali,yana tsarkake ubangiji,yana sake miqawa Allah godiya. Duk da bai isa inda ya dace ya isa ba,amma ko a iya nan ya fahimci abinda zai sanya duk namiji ko.macen da suka kuskura suka fara zina a rayuwarsu zai wahala su daina. (Duk runtsi.....duk runtsi,duk yadda za'a je a dawo ka/ki yiwa kanki katanga da zina,karki kuskura karka kuskura ka yarda ka dandanata,ka jira halal time......in halal way kuma,Allah haula da zuri'armu duka ka nesantamu da ita). "Alhamdulillah......alhamdulillah" Yake furtawa a hankali. Wani girma da tsoron Allah yana sake ratsa zuciyarsa......imani na gaske da yaqini,irin karamcin Allah daya yiwa bayinsa. *zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 08187255862 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 08187255862 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 42* Duk abun daya ne,amma saboda Allah ya karrama dan adam ya sanyashi ya zama ta halastacciyar hanya. Cikin girma mutunci da karamci da amincewar iyaye,bayan ka biya wani abu cikin kalmomin Allah da sunnar manzonsa S A W. Yana jin sanda ta fito,ta dade tana lallabowa gami da takawa a hankali tanason saka kayanta. Bata lokaci yayi,yayi kaman bayan gurin,bai juyo ba ya barta ta shirya duk da tsorace take,sai daya tabbatar ta hau gadon sannan yabar bakin gurin,ya tako a hankali da wani irin sanyi da nutsuwa yaja duvet din ya lullubeta. Samun kansa yayi da sunkuyawa daidai goshinta. Lite kiss ya ajiye mata,ya taka da baya da baya a hankali ya kashe duk wutar dakin,sannan ya juya yana barin dakin da wani abu daya soma nauyi da girma a qirjinsa,wani abu da baisan meye shi ba. Duk da taji fitarsa amma ta kasa motsi tun bayan da kiss dinsa ya zauna mata daram a goshinta. Ta sauke nannauyar ajiyar zuciya tana tuna komai daki daki. Takai hannunta saman wuyanta... Kunnuwanta,qirjinta,cinyoyinta dama bayanta. Duk inda takai hannun saita tuna da wanne irin yanayi nasa hannun ya sauka a gurin,saita runtse ido sosai tana damqe pillow din da take kai. Sai a yanzun takejin wancan feeling din daya kamata ta jishi a dazu sosai tsoro ya hana. "Biftuuuuuuu" Taji wani sashe na zuciyarta ya kirata da qarfi,saita cusa kanta cikin pillow tana rasa me zatayi?. Anya bata fara hauka ba?.....bata fara samun matsalar kwanya ba?. Me yasa komai dake tattare da ita yake sauyawa?,me yasa komai nata yake sauya kanshi?. Ina wannan ra'ayin nata?....ina dukka dokokinta da tsarinta suka tafi? Wannan malaminne fa?,wannan malaminne fa kamar dai sauran malamai data sani. "Ba kamar sauran malamai ba akhnan.....ba kamar sauran ba" Wani sashe na zuciyarta ya shiga gaya mata a hankali. Batayi saurin qaryatawa ba,samu kanta tayi da sake tariyo komai nasa. Ranar farko data fara ganinsa......yadda izzarsa bata bari a takashi. Yadda bai yarda da wulaqanci qansqanci ko tazarci ba. Girman muqami na mahaifinta da dukka kyanta bai sanya ko sau daya ya shiga sahun mazan dake nacin shiga Rayuwarta ba,sai yanzu.....sai yanzu da igiyar aure ta qullesu guri daya. Saka dukkan qarfinta tayi tanason wancakali da tunanin ko zata samu bacci,saidai duk inda ta motsa.....duk yadda ta juya ba abinda hancinta yake shaqo mata sai wannan qamshin nasa. Wannna qamshin dai.....qamshin da tasake ji a ranta ko yaya ne zatayi ta mallaki wannan turaren. "Ta yaya biftu?" Ta tambayi kanta da kanta tana tsaiwa cak. Ba abinda yake dawo mata a kai sai tafiyarsu....wannan tafiyar tasu. "Waye shi?" Ta sake tambayar kanta. Iko da take gani tattare da komai nasa yana sake jefata a tunani tarin zaquwa da son sanin WAYESHI?. Baya bayyana iko da kansa.....amma ikonsa ne yake magana da kansa ba tare da haisam din ya furta komai ko ya nuna komai ba. Wani abu ya sake ratsa zuciyarta sanda ta kwantar da kanta saman tafin hannunta. Daidai da tafin hannunta qamshinsa yake. Kowacce gaba ta jikinta tuna mata dashi take. Tana iya jin hannuwansa ako ina na jikinta tamkar a yanzunne yake yin komai. "Ya salam,ya Allah" Ta fada a hankali tana lumshe idanunta,tana kuma jin yadda bugun zuciyarta yake sauyawa da wani irin sauri. Da gaske bacci ya qauracewa idanunta,duk inda ta juya qamshin da batasan haka yake ba sai a yau din. Bedsheet dinta.....duvet dinta....pillows din dake kan gadon gaba daya,uwa uba jikinta da batasan me ya zaunar da qamshin ba bayan wankan duk da tayi,saita yanke ta sake wani wankan ta kuma canza muhalli ko zai ragu. Wankan ta sake,ta kuma hado da alwala ta sauya wasu kayan,saidai still ba abinda ya sauya wannan,sai kawai ta dauki abun sallah,ta koma bakin haram view ta shimfida ta tayar da sallah nafila. Raka'a hudu kawai idanunta suka fara nauyi,ta zauna a gurin a hankali. Dabi'arsa ce istigfari,sau tari zata jishi yana yinsa can qasan maqoshinsa,a hankali sai taji bakinta ya kama....daga wannan yanayin daga wannan lokacin daddadan bacci me cike da mafarkansa a wancan yanayin na awannin dazu ya sureta. ★★Kwata kwata bata taba kawowa zai sake iya hada idanu da ita ko tunkararta ba. Sai gashi gata cikin wani irin yanayi na nutsuwa gaban ka'aba suna dawafin ban kwana(ba wajibi bane a umra,ya zab'ar musu suyi dawafinne kawai). Wani irin nutsuwa ta dinga shigarta,wani irin yanayi,saita samu kanta tana koyi da yadda yake aiwatar da dukka motsinsa na ibada tana qoqarin kwaikwaya. Duk sanda ta daga idanu ta kalleshi abun jiya yake fado mata,wani irin satar kallo take masa don tasan muddin ta bari ya kamata tana kallonsa qila kunya ce ajalinta. A yanzun daya nutsu yake zaune yana addu'o'insa sai take satar kallonsa. Wani iri kamala tana sake lullubeshi,ta dauka wannan kwarjinin da yake mata.....wannan cika idanun da wannan haibar da take cika mata idanu zasu zagwanye daga abinda ya faru a jiya,amma sai taji babu ko daya data girgiza,babu ko daya data tabu,saidai mamakinsa kawai da takeji cikin zuciyarta. Wani abu d'aya data lura dashi.....wanda har sai daya sanya taji kanta ya wani kumbura. Kaffa kaffan da yakeyi da ita wanda ya ninka farkon shigowarsu makka. Hannayensa yake sanyawa hagu da damanta ya kakkangeta daga kowanne namiji da zai matso kusa da ita. Har sukayi dawafin nan bakwai bataza ce iya cewa ta hada kafada da wani namiji guda daya ba. Koda zamzam da zata sha yana tsaye bisa kanta bayan ya matso ya bata da kanshi,hakanan a yanzu da suke gaban ka'aba daga dan nesa inda kowa ke zaune yana gabatar da addu'o'insa. *AGADEZ* *_SULTANE PALACE_* K'arfe takwas na dare ne,wanda yayi daidai da qarfe goma na dare agogon saudiyya. Masarautar tayi wani irin shuru,shurun da kana jinsa zakasan ba shuru bane na al'ada,ba kuma shuru bane dake nuni da lumana da nutsuwar duk wani d'an masarautar. Kusan ba cikin masarautar kawai ba,AGADEZ gaba daya cike take da alhini lalurar data kwantar da sarkinsu me adalci.....sarkin da suke mata wata tsaftatacciyar soyayya saboda kulawa da damuwa da yayi da matsalolinsu SULTANE MUHAMMAD HAMMUD na biyu. A daidai wannan lokacin take takawa cikin izzar da har yanzu takejin ba wani abu da zata bari ya taba wannan izzar......duk da kuwa har yanzu ta gaza gamsuwa da kallo da gaisuwa dama tarbar da hadiman gidan sukayi mata. Kwanaki bakwai kenan.....kwanaki bakwai din data yisu a hannun hukumar hana sha da fataucin miyagun qwayoyi. Kwanaki bakwai din da suka zame mata daidai da shekaru dubu bakwai wajen tsaho da ganin baqinsu. Ba'a ci zarafinta ba,ba'a hanata muhalli da abinci me kyau ba......amma tashin hankali da masifar data shiga na kula da yaduwa da labarin kamata da tsareta da yayi cikin niger gaba daya yafi komai zame mata barazana. Da kowanne motsi na ma'aikatan hukumar take fahimtar komai. An shirya komai ne kawai don a kawota nan a b'ata sunanta.......to amma babban abun mamakin......ya akayi birnannen sirrinta?,boyayyar harqallarta?,tsohuwar sana'arta da tafi kowacce mallaka mata baqaqen kudade lullubin sirrinta ya yaye?. "Sheikh muhammad haisam......alsaamit" Sunan daya dinga maimaituwa a cikin kanta kenan. Ta sake gasgata hakan sanda aka saketa bayan kwanaki bakwai da sunan an mata alfarma,zasuci gaba kuma da bibiyar case din. Kenan sun mata kisan mummuqe kenan?,sun bankado komai don su tona asirinta su zubda kimarta a idanun duniya bawai don su kamata ba?. "Me yake shiryawa?" Tambayar data kwana tana zirga zirga kenan a kanta bayan ta dawo dakinta ta kuma gagara samun amsar,wanda daga qarshen dare kwanyarta ke gaya mata. "Ki shirya yadda zaizo hannunki......yadda zaki mallaki qudurinki na qarshe.....ki cinnawa burinsa da dukkan ikonsa wuta.....wutar da bazasu iya kasheta ba har qarshen rayuwarsu". Wannan shine shawarar da zuciyarta ta bata. Shawarar data rasa ta inda zata kamota sai a yanzu da take kan hanyar amsa zaman tattaunawa akan makomar masarautar game da lalurar sultane. Wani murmushi ta saki me sauti,har sai da hadiman dake take mata baya suka kalli juna. (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) "Kwanciyar sultane......itace zata zame min hanya mafi sauqi da zan kammala komai......ya kamata YA MUTU ya qarasa mutuwa" Ta fadawa kanta tana jinjina kai da jin gamsuwa da wannan shawarar. Da izzar da a yau takejin kamar ta raunana take takawa cikin dogon dakin tattaunawar dake dauke da kujeru na zama iya adadin 'yan majalisar sarki da sauran spare kujeru koda za'a buqaci zama da wasu mutane na daban,kaman yadda a wannan zaman aka buqaci zuwan yakumbo,nannie.....morsa safiyya,da mammina din,sai tsoho me ran qarfi kaka ga morsa safiyya daya zama kamar d'an gida. Kallon da take gani a idanun wadannan mutanen,kallo ne daya sanyata jin wata siririyar muzanta ta fara saukar mata,amma daga baya taji ta ware bayan kawo gaisuwa da wazeer da sauran manyan fada sukayi kaman yadda aka saba. Wani kallo ta ajewa morsa safiyya,tayi sanyi sosai yanayinta ya nuna hakan. Ba qaramin tabata ciwon sultane yayi ba,wani irin ciwo daba wanda ya gaya musu me yake damunsa?. Yanzun nan kuna magan dashi,bayan awanni sai ace babu shi ya shiga coma. Wata irin coma da duk bayan awanni yakan iya tashi,ya sake komawa bayan awanni. "Ya Allah,idan har wannan itace qaddarata a rayuwa,Allah ka bani ikon cinye wannan jarrabawar.....ba khadeeja......ba safeena.....yanzu kuma sultane?" Iya tuna wannan kawai ya sanya hawaye zarto mata,hawayen daya sauka a idanun mammina. Wani irin dadi taji yana mamayarta,ta sauke murmushin nasara. RAUNI wani abu data jima tanason jefawa hade da tsoro a zuciyar safiyya amma bataci nasara ba saboda kalar zuciyar dake qirjinta,saidai yanzu gashi cikin ruwan sanyi komai yana zuwa daki daki,da alama wannan karon duk da aikin na qarshe ne ya kamata yazo da zafi zaizo mata a sauqaqe. Dogon maganganu da tattaunawa akayi,kafin daga bisani aka gangaro kan ainihin dalilin haduwarsu. "Ya za'ayi da riqon qwarya na sarautar AGADEZ?" Wani abu ya harba a zuciyar mammina. A irin wannan lokacin karon farko taji inama ace ta haihu?,inama ace tana da d'a?,koda wannan d'an bana sultane bane ta mallakawa sultane shi,da tuni yanzu wannan damar cikakkiya tata ce. Tsanar safeena ta sake cika mata zuciya da ruhinta gaba daya. Safeena ce sila.....Ahmad tabbas inda ba safeena d'anta ne....rabonta ne,ita zata haifeshi,tsinanniya safeena ta qwace mata wannan damar. "Ina ganin a wannan lokacin muna buqatar muji ta bakin sheikh haisam,don shima a matsayin d'a yake a gurin sultane" Nannie ta fadi,maganan kuma ya zaunawa kowa,take kuma wazeer ya soma lalubar haisam din Wani makirin murmushi ta saki tana sake gyara zamanta hankalinta kwance. Akwai mutane da yawa da take hasashen su za'a bawa,inde hakanne sama da mutum goma a cikinsu data lissafa kowa a cikinsu tana da yadda zatayi dashi. Manyan idanunsa dake lumshe ya bude a hankali jin alamun wayarsa dake jikinsa. Ya zarota yana duba me kiran,sai ya miqe a nutse a hankali yana fadin "Kiyi addu'a,ki roqi Allah dukkan alkhairi na duniya dana lahira.....ina zuwa" Ya fadi a nutse yana danyin nesa kadan da ka'abar saidai bai gaza hangota ba daga nan inda yake tsaye. Shuru tayi maganansa tana mata yawo cikin kunnuwa. Tana lissafa iya adadin abinda ta roqa daga zuwansu garin zuwa yau da suke shirye shiryen fita daga qasar. "Shine kawai ya rage.....baki bawa Allah zabi ba.....baki roqi Allah komai a kansa....baki magana a kansa ba,bakice komai wa Allah a kansa ba" Wani sashe can qasa ya yunquro daga zuciyarta yana rad'a mata.. *zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 08187255862 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 08187255862 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 43* Idonta ta lumshe sanda muryarsa ta cika Hall din cikin cikakkiyar sallamar data sanya kowa ya nutsu sosai tamkar yana gabansu. Cikin girmamawa suka gaisa da wazeer,sannan ya gabatar masa da dalilin kiran. Boyayyen murmushi ya saki,ya soma miqa gaisuwa ga dukka wani babba da yake hasashen yana gurin. "Ra'ayinka mukeso muji". Cikin nutsuwar nan tasa ya soma bayani. "Allah S W T daya sanya mana 'ya'ya cikin hikimar bamu su shine,saboda mudin gajiyayyu ne,'ya'yanmu sune makwafinmu,sune qarfinmu,sune hotonmu....sune kuma masu iya dorawa daga inda qarfinmu ya tsaya......a yanzu alhamdulillah sultane yana da magajin da na gamsu zai iya riqe agadez.....zai iya kwatanta abinda sultane yakeyi bisa jagorancinku shawarwarinku da dafawarku.......bisa shawarata da hangena.....ahmad shine yafi cancanta yahau wannan kujera" "Saboda ka raina furfura da shekaru na mutanen da suke gaba da ahmad din wajen gogewa da iya sarauta?,ta yaya duk manya da dattijai da muke dasu ace ahmad qaramin yaro zaa bawa sarauta?,wannan baya cikin tsarin doka ma,yaushe duka duka ya dawo da zai haddace tsarin sarauta har yayi jagoranci?" Mammina ta furta cikin harzuqa. Kaman yadda haisam din yayi shuru cikin nutsuwa,haka hall din ya dauki shuru,shurun daya sakata ta tsargi kanta da kanta saboda gani data fara yi kaman kowa idanunsa yana kanta. "Bazakuce komai dashi ba?" Ta fada cikin son danne tsarguwa da nauyin data ji. Wazeer ne ya gyara zamansa sosai yana dora idanunsa a kanta. "Mun gode sosai sheikh haisam.......shawararka ta karbu,kuma in sha Allah bazamu kunyata sultane ba,Ahmad ya dawo a daidai,zamu dafa masa har sai ya cimma gaci,saboda dukkaninmu ya fimu cancanta,alamun nutsuwarsa kawai tana bamu tabbacin zai iya" "Na gode sosai.....na gode da fahimtata da akayi" Haisam.ya fada a girmame yana kashe kira. Wani ajiyar zuciya morsa safiyya ta sauke hawaye yana sauko mata sanda kowa ke rattaba hannu gurin yarda da amincewar cancantar ahmad akan mulkin AGADEZ. Ta sake girmama hukuncin Allah me juya al'amura a yadda yaga dama. Wa ya taba tunanin sake samun ahmad a raye?,har wannan rana tazo da zai hau sarautar mahaifinsa koda kuwa riqon qwarya ne. "Zakaran da Allah ya nufa da cara" Ta furta a hankali,saqon kuma yakai kunnen mammina,saqon da ta fadeshi ne kawai saboda lamarin ya mata kama da hakan,maganan kuma ya dauki hankalin mammina daga mummunan kallon da take saukewa wazeer. Yadda ya bata amsa a dazun kamar akwai wani qulli a ransa shima game da ita,me yasa bata tana sakashi cikin target dinta ba?. "Yanzu ma bata baci ba,ban makara ba" Ta bawa kanta da kanta amsa,sai murmushi ya biyo baya ta jinjina kai. "Kun sake sakashi a qabarinsa a karo na biyu.....qabari kuma duk wanda ya shigeshi sai ranar tashin qiyama shida fitowa" Ta fada can qasan ranta. *ETHIOPIA* *_ABA JIFAR INTERNATIONAL AIRPORT (JIMMA AIRPORT)_* Cikin shigar da tayi daidai data 'yan uwanta,cikin yanayin da bai banbance matsayinta dana su Aanani ba take zaune cikinsu,cikin ayari ne musamman dake dakon isowar prince sheikh muhammad haisam aba jifar. Tun daga ranar da labarin YAYI AURE ya shiga kunnenta,idan tace tayi cikakkiyar lafiya ta zuci data gangar jiki to tabbas tayi qarya. Daga wannan rana BACCI ya zame mata wani abu me wahalar samuwa ga idanuwanta.....daga wannan rana suka qulla abota da kukan zuci....daga wannan rana ya zamana ba wata rana da zata fito ta fadi bata tsaya gaban madubi ba.....bata kalli kanta ta tambayi kanta da kanta. "ME KIKA RASA SAAMEE?.....MEYE BAKI DASHI DA KIKA GAZA FARAUTO SOYAYYAR CAPTAIN SHEIKH?" Wata tambaya guda daya data gagara samun amsarta.....sai kuma wani rashin tabbaci na "Kin haqura?.....zaki yarda makamanki?,zaki tabbata mara nasara ta hanyar barwa wata shi?" Wannan tuhume tuhume ne da zuciyarta ke yawan yi mata su amma ta gaza bawa kanta da kanta amsa. A daidai wannan lokacin sai takejin wani ciwo yana qulle mata a qirji. A duk inda ta ajiye idanunta zallar farinciki take gani a fuskar kowa na dawowarshi.....zumudi da walwala da fatan isowarshi cikin ahalin aba jifar da matar da zata yita amsa sunanta da nashi a maqale "Matar shiekh muhammad haisam... Yarima me jiran gado" Ta lumshe idanunta muryarsu Aanani na mata amsa kuwwa. Ta kasa bude idanunta saboda ba abinda take kalla sai walwalar dake saman fuskokinsu. Sanda qugun jirgin da yake bata tabbacin jirgin da suke dako ne ya iso.....a sannan ta bawa kanta da kanta amsar tambayarta..... Ba zata iya jurewa ba.....ba zata sallama haka da sauqi ba......ba kuma zata yarda tayi asarar abinda ta rayu shekaru kusan uku tana burin mallaka ba. Saita samu kanta da miqewa tsam.....a sannu a sannu ta soma ja da gaya tana bacewa idanun duk wanda zai iya ganinta,tana barin dakin jira na musamman din da aka bawa iyalin me martaba ibraheem aba jifar don jiran isowar SHALELEN QASAR HABASHA......wanda airport din ta cika da manyan mutanen dake dakon isowar haziqin ma'akacinsu......sannan masarauta ke dakon isowar magajinta. Ko ba'a gaya maka ba,koda kuma baqo ne kai cikin garin jimma idan ka kalli aba jifar international airport din zakasan cewa akwai babba kuma muhimmin abu da yake faruwa cikin airport din,saboda wasu irin lafiyayyun motoci dake jere bisa tsari masu kama d'aya dukkaninsu suna jiran isowar private jet din dake dauke da prince sheikh muhammad haisam aba jifar da matarsa. Dukkanin mutanen dake airport din suna jiran isowarsun suma cikin tsari suke,fuskokinsu cike da walwala annashuwa da hira kadan kadan me nuna nutsuwar kowannensu. HUSSAM kyakkyawan matashin mallakin qabilar oromo,kuma jini ga sheikh haisam din,kusan shine jagora kuma shugaba na tafiyar gaba daya. Kai kawo yake yana duba lokacin da yake a rubuce na saukar jirgin. Kamar ya matsu yaga isowar captain obbo......ya matsu idanunsa su sauka akan d'an uwan nasa da macen da tayi nasarar wuf dashi. Cikin nutsuwa private jet din ke sauka da wani irin yanayi daya sauka saman zuciyar akhnan wadda ke zaune cikin kujerun alfarma da jirgin ya mallaka. Iya kujerun da su kadai sun isa su gaya maka luxury din dake cikin jirgin koda baka taka qafarka zuwa ko ina ba. Yau jikinta yafi yin sanyi sama da ko yaushe....a yau da jirgin ke daukosu daga jidda zuwa jimma sai takejin komai yana kwance mata fiye da ko yaushe. Wani irin royalty take gani.......wani irin yanayi na zallar girmamawa da wani irin respect. High luxury na rayuwa daya sake damalmala mata lissafin data fara qullawa kan WANENE HAISAM DIN. Tafiyar awa shida ce.....amma banda sallah da yace tayi ta shiga toilet ta fito tazo tayi sallar bata sake motsawa ko ina ba. Hasalima yau da suke zaune guri daya na awanni masu yawa ya zame mata kamar wani surukinta. Tun shekaran jiyan da wannan abun ya gilma.....tun ranar bata sake bari idanunta sun shiga cikin nasa ba. Haka kuma takejin nauyin yana sake daduwa a kowacce rana,da mamakin yadda yake komai kanshi tsaye ba wan kwana kwana kamar komai ma bai taba faruwa ba. Lumsassun idanunta ya soma budewa a hankali bayan ta tabbatar jirgin ya isa ga qasa......qasar da takeji a ranta a nan zata rayu?......na tsahon wanne lokaci ne?,wacce kalar rayuwa zatayi?,dawa dawa kuma zata rayu din?. Tambayoyin da suke sanyayar mata da dukka gabbanta. (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) Falaak take tunawa taji sanyi da nauyin dake qirjinta ya ragu,saidai sam ba zatace taga falaak sau biyar cikakke ba tun daga barinsu agadez zuwa yanzun da suke sauka a jimma cikin jirgin da iya ita dashi ya dauko kamar dai wadancan jiragen. Akwai banbanci me yawan gaske na zahiri tsakanin wadancan jiragen da wannan.....nisan tazarar daya sake luluqa tunaninta a kanshi. Idanunta duka ta qarasa warewa jin jirgin ya tsaya. Bata tsammaceshi a kusa da ita haka ba,don haka kanta tsaye ta ware idanun nata fes sukayi kyakkyawan matsugunni cikin nasa kuwa. Zaune yake sosai a kujerar da take facing tata kujerar.......da wannan kayan da tunda ya fito daga dakin hotel dinsu na raffles makkah ya dauki idanunta da hankalinta,saidai a yanzun takatsantsan take da komai daya shafeshi a yanzun,bata yarda wani dogon kallo ya hadasu ballantana ya kama idanunta. Ya zuwa yanzu ta gama sallama.....idanunsa ba.....burgeta suke,wani irin burgeta sukeyi,tana jin kamar a duniya sune idanu mafiya kyawu na farko data taba gani. Bata yarda ta kalleshi kai tsaye ba,saita sauke idanunta akan dogayen yatsunta farare tas da har yanzu sauran lallen jiki bai fita ba. Shuru ya ratsa tsakaninsu,wani irin shuru da batasan me hakan yake nufi ba. "A jirginma.....a qasarsa ma sai ya nuna izzar?" Ta fada can qasan ranta tana jin alamun idanunshi a kanta. Da gaske ita yake kalla,zara zaran yatsunta da take murzawa a hankali. A duk sanda zai kalli hannuwanta sai tuna yadda yatsunsa suke narkewa cikin nata duk sanda zai kamasu. A duk sanda ya kallesun sai yaji kaman ya kamasu ya maqalesu cikin nasa. Taushi da dumin da yakeji a jikinsu na dabanne. Rigar jikinta wata irin luxury abaya ne da aka sanya dollars masu nauyi aka siyeta cikin haramin makka. Sun mata wani irin kyau.....wani irin black color me daukan idanu. Yana jin bazai iya barinta ta fita a haka ba......yana jin kamar duk mutanen jimma suna bakin qofar jirginne suna son ganin fuskarta. Idanunshi ya zare yana jin wani numfashi me nauyi yana subuce masa. Ya saka hannunsa yana yaye labulen window din jirgin don ganin yanayin da farfajiyar ajiyar jiragen take ciki. A kanta idanunsa suka sauka......Khansaa Moti ibraheem aba jifar. Jinin sheikh muhammad haisam,kyakkyawa macace 'yar qabilar oromo na asali,diya ta farko daga tsatson ibraheem aba jifar da khadeeja yunnus jallata. Sanye take da wata tattausar lafaya wine color,wadda aka yiwa ado da olive green me wani irin nau'i me daukan hankali. Kyakkyawa ce ta gaske......wadda jinin moti aba jifar ke gwada kansa sosai a jikinta. Da kallo daya kawai idan kayi mata zaka tabbatar da cewa basarakiya ce.....akwai sarauta da mulki dake zagayawa cikin jininta. Ita kadai yake hangowa tana takowa da kan matattakalar jirgin. Kallo daya ya yiwa fuskar 'yar uwartasa ya hangi wani irin murmushi kwance saman fuskarta dake kama data moti sak da sak. Daga matakalar qarshe ta dakata,cikin izzar nan data zame musu natural a halittarsu,ta miqa dogon hannunta dake shirye da wasu irin awarware na iko tana karbar kyakkyawan qaraman luggage din dake hannun hadimarta,wadda ke ajiye qafarta duk inda khansaaa ta ajiye. "Ki koma qasa,zamu fito yanzu" Tayi maganan da iko sosai cikin muryarta. Rusunawa tayi ta miqa mata akwatin,sannan ta soma sauka da stairs na jirgin tana komawa inda sauran mutanen ke tsaye jikin matakalar cikin jerin sahu guda biyu hagu da dama. Murmushi ta sake saki sanda crew din ke bude mata qofar tana mata nuni da inda su haisam din suke cikin girmamawa,ta jinjina kai kadan sannan ta fara takawa a nutse fuskarta shimfide da wata tattausar fara'a tana nufar gurin. *zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 08187255862 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 08187255862 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 44* Sakin labulen yayi,a jikinsa yaji alamun shigowarta jirgin,sai ya miqe a nutse yana gyara thobe dinsa,sannan ya fara takawa zuwa dan qaramin kyakkyawan curtain din da shine kawai zai haba khansaaa ganinsu. A tare suka daga labulen shi da ita,dukkaninsu fara'ar fuskarsu ta kasa boyuwa,musamman khansaaa da sai da jerarrun fararen haqoranta suka bayyana. "Captain obbo" Ta fada tana kallonshi cikin dariyar dake nuna zallar qaunar juna dake tsakaninsu irin na 'yan uwantakar data samu kulawa daga iyaye,da soyayyar dake nuna zallar hadin kai. "Malka khansaa(prince khansaaa)" Ya amsa mata cikin yanayi na sakewa da juna da kuma tsokana. Murmushi sosai tayi me hade da sauti "Xiqqaa koo(my little one)" Ta amsa masa tana dubansa kai tsaye. Ya sani,tanason tsokana ne kawai,don tana cikin wadanda mamakinsu bai buya ba sanda akace musu yayi aure tun daga agadez. "Na sameku lafiya?" Ya sake tambayarta yana dubanta. "Alhamdulillah.....amma dai da farko duk ba wannan ba.....kasancewar munyi kewarka irin wadda bamu taba yi ba,amma zan gaya maka gaskiya a wannan karon.....bata taka muke ba.....baquwarmu muke marabta ba kai ba.....ko zaka iya dan yimin haquri na qarasa naga wannan kyakkyawan ruhin da yayi nasarar sace wannan zuciyar da aka gaza budawa kowacce mace ita?". Murmushi dole ya subuce masa,tun a nan?,a haka ma khansaaa mutuniyarsa ce sosai.....abokiyarsa....kuma ta wani fuskan yadda take treating nasa yasa yake mata kallon nanay ta biyu? Tun a nan ta gaza boye tsokanarta?,ina ga tarin cousins dinsa da suke jiransa da sauran abokai?. Baice mata komai ba,yayi taku biyu baya ya matsa yana bata hanya. Da murmushinta ta rabashi tana wucewa,dukkanin idanuwanta suna kan akhnan. Kanta yana qasa daga sanda taji baquwar muryar mace suna magana dashi da wani yare da bata ganewa. Ta lumshe idanunta,wannan yaren kawai ya isa ya bata tabbacin zuwanta wata duniya ta daban. Ya isa ya gaya mata a yanzun ita ba wancan akhnan din bace.....ba a agadez take ba....ba'a Niamey take ba,ta shigo wata duniya ne ta daban. Mamakin saurin amintar da sultane da yayi,da har ya aminta ya dauketa ya damqa masa ita ba tare da sanin ainihin tartibin ina zaikaita ba?,wayeshi?,ina zai ajiyeta a rayuwarta ta gaba?. "Keessummaa keenya” abinda khansaaa ta fada kenan da wannan 'yar gayun muryartata me dadin sauraro. Sautin kadai shine ya fusgi hankalin akhnan ta daga kanta bawai donta gane me take fadi ba. A take idanunta ya sauka kan fuskar khansaaa. " Subhanallah" Ta fada can qasan maqoshinta tana hadiye wani abu. Shige idanun nan nasa ne take dashi,banbancinsu nasa yana da wani irin shape da bata ganshi tattare da wannan ba,hakanan wadannan nata idanun an zizara musu kwalli daya sake qawata idanun. Jar lafayar jikinta na nuna zallar iko,don duwatsun da aka shiryawa lafayan kadai magana suke da madaukakin sauti zuwa nuna ainihin tsada da darajar suturar jikinta. Hannun khansaaa data miqo mata tana sake mata wani amintaccen murmushi tabi da kallo,wani tattausan hannu da aka zanawa kyakkyawan zanen jan lalle wanda adon flowers din sukasha banban dana yankin agadez nesa ba kusa ba. "Afaan Ingiliffaan ishee waliin dubbadhu(ki gwada yi mata magana da English)" Yace da khansaaa data rusuna a gaban akhnan. Kai ta daga ta kalli haisam,ta saki murmushi tana maida dubanta ga fuskar akhnan,wadda sai yanzu taga fuskarta sosai saboda ta tsugunna ne ta gabanta. "Maaaa shaaaaa Allahhhhhh......subhanallah.....captain?" Khansaaa ta fadi sanda idanunta ke saman fuskar akhnan idanunta suna nuna zallar daukan hankalinta da akhnan din tayi. Basarwa yayi,don kafin tace komai yasan akan me zatayi magana,yanayinta ya karanta masa,sai ya fara takawa kawai yana ficewa daga gurin,abinda ya sanya khansaaa sakin dariya tana maido dubanta ga akhnan. "Mijinki miskili ne.....yana da wahalan sha'ani wani lokacin,ina fata kin fahimci hakan?" Ta fada da harshen turanci tana kallon akhnan. Sai a sannan taji kaman an sassauta mata d'aurin da akayi mata,ta fahimci abinda Khansaaa tace,saidai kuma nauyin da takeji nata haka kawai ya sanya ta kasa maidawa,sai wani qaramin murmushi data saki tana sake karantar Khansaaa a fakaice. A jikinta takeji kamar JININ SARAUTA ce ita....wasu motsi nata yana mata kama da mutumin daya fito daga royal family. "Ina miki jinjina......ina kuma sake sallama miki da yadda kika bude wannan zuciyar me tsananin kafiya....zuciyar data shekara talatin da biyar ba macen data dauko maqullinta daidai ballantana ta samu daman budeta" Ta sake fadi da wani yanayi na raha cikin muryarta. Murmushi akhnan tayi qoqarin maida matan,amma maganganunta suna sauka saman zuciyarta a hankali. "Kowa so yake yaga wacce me sa'ar ce tayi wannan gagarumin aikin?" Khansaaa dake riqe da hannun akhnan tana jin kamar hannun rumaisa ko na Aanani ko noorah ne ta riqe ta fada tana qaramar dariya. Dariyar data sa ya akhnan sakin murmushi a nutse tana sake sadda kanta qasa,haka kawai takejin wani irin nauyin matar da ta kasa riqe sunanta da taji ya kira. "Bazai taba bari ki fita a haka ba,koda al'ada batazo mana a haka ba,idan ban takuraki ba,ko zaki shiga dakincan ki canza kayan jikinki?,saboda zamu wuce palace learning residence kaman yadda yazo a al'ada" Yadda take maganan cikin kulawa da taushi ya sanya akhnan binta da kallo. Akwai sarauta sosai a yanayinta,amma akwai wani sauqin kai da martaba me yawa a kallonta da maganganunta,bata gane me take nufi ba illa dai batun canza kayan kawai. "Akwai wanda za'a kira miki don ta taimaka?" Shuru ta danyi,kafin ta lumshe idanunta ta budesu a hankali sannan tace. "Birra" Murmushi Khansaaa ta saki,karon farko da taji muryar data matuqar burgeta ba. Ta murmusa a nutse tana dannan wani madanni jikin wani lafiyayyen agogo dake daure a hannunta,sautin muryar akhnan na ratsata,laushi da wani irin aji dake tattare da ita. "Birra" Kawai akhnan taji Khansaaa din ta fadi,cikin qasa da minti daya qofa ta bude birra ta shigo. "Ki tayata ta shirya" Khansaaa ta fadi cikin yaren oromo. Ga mamakin akhnan sai taga birra ta gyada kai,a maimakon taga ta rude tana neman ma'anar abinda akace mata,sai taga ta dauki luggage din ta taka zuwa dakin "A fito lafiya" Khansaaa ta fada cikin girmamawa da harshen English. Bata da wani zabi saita juya tana bin bayan birran. (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) Tunda taga dakin yanzunne shigarta ta farko. Tsoro takeji ta shiga bacci ya kamata ko wani abu makamancin haka wani abun ya faru da ita,shi yasa ta shanye dukka awannin a zaune cikin luxury sofas din. Tasha mamakin irin suturar da taga birran na fitowa da ita daga cikin luggage din. Harkar sutura ce sana'arta....bangarenta ne. Duk wani fabric da zare yarn da dutse me tsada ta sanshi. Ta sake qarewa rigar kallo da kyau,sai taga tayi mata kama sak da sabuwar rigar da companyn Elie Saab sample din da ake saka ran zasu fiddashi shekarar 2030. Batace komai ba,tana tsaye kawai birran ta shiryata tsaf,sannan ta nadeta cikin ni'imtaccen yadi na alfarma,wanda ya qarawa rigar kyau a jikinta. Mirror ta ajiye mata yadda suka saba a kowacce shiga da zatayi a agadez,ta taka a hankali ta matsa gaban mirror din. Wata akhnan daban take gani ba irin wadda ta sani ba,wata akhnan ta daban ba princess of agadez ba. Wata akhnan daga wata qabila daban take gani,wata akhnan da kayan da take sanye dashi ya zame mata wani irin abu na daban daya fidda wata irin sigar kyau tata,duk kuwa da cewa ta lullube kowanne abu nata da zai iya zama al'aura. Haka kawai taji jikinta yana yin sanyi,hakan kenan yana nufin ta sauya qabila?,ta sauya qasa da al'umma gaba daya?. "Zan iya shigowa?" Taji muryar Khansaaa daga bayan qofa. "Eh" Ta amsa mata a sanyaye tana waiwayowa gaba daya. "Fatabarakallahu ahsanul khaaliqeen" Ta fada murmushinta yana sake qaruwa. Hannunta ta miqawa akhnan tana fadin "Duk kowa yana waje yana jiranki,lallai dole captain obbo ya buqaci a boye wannan kyan,mu kanmu kishinmu yake ballantana halal dinsa?" Ta fadi tana murmushi sosai. Murmusawa kadan tayi don kada tabar Khansaaa da fara'arta ita kadai,saidai can qasan ranta,can qasan zuciyarta tana jin wani shafi yana budewa na sanin sabbin halaye da dabi'unsa da bata sani ba a baya. "Sunana Khansaa ko hasnaa.....duk wanda kikeso zaki iya kirana dashi.....nice yaya ta biyu ga captain sheikh,kuma aminiyarsa". "Captain.....sheikh....obbo" Duka sunayensa ne?. Zata iya cewa sunan sheikh dinne kawai ba baqon suna ba a wajenta,amma gaba daya sauran baqi ne a gurinta. Ta daga kanta a hankali sanda suke dab da bakin qofa,sai idanunta suka sauka a kanshi. Yana tsaye fuskarsa na fidda wannan hasken,wannan kwarjinin da haibar shimfide saman fuskar tasa,saidai kuma mayen waya....mayen waya ne kaman yadda ta soma laqaba masa. Idanunsa suna kan wayar yana danne danne. "Bismillah captain" Hasnaa'u ta fada tana miqawa haisam hannun akhnan. Sai a sannan ya daga fararen idanunsa ya saukesu a kanta. "Ya hayyu ya qayyum.....ya zaljalalu wal ikram" Ya fada can qasan maqoshinsa adams apple dinsa yana motsawa sama da qasa. Wata mace daban yake gani.....haihuwar qabilar oromo.. Wata matashiya yake gani daban ba khadeeja muhammad hammud ba cikin tufafin al'ada na sarautar jimma oromo. Sai yaji wani sanyi yana ratsa sannan jikinsa.....wani abu yana mamaye ilahirin jikinsa,ya dauke idanunsa a hankali yana duban gaban jirgin da mutanen da suke jiran saukowarsu. "Su waye da waye a waje?" Ya tambayi Khansaaa da yaren oromo,da wani irin yanayi da kasala ke bibiye da sautinsa,kasalar da yanzu yanzu ta saukar masa. "Daga nan yan uwa ne na kusa,daga can farfajiyar airport din kuma bazance ga adadi ba". Idanunsa ya lumshe a hankali saman fuskar Khansaaa sannan ya budesu. Da iya hakan kawai da yayi ta iya karantar yanayinsa,ta kuma iya gane me yake kaikawo cikin zuciyarsa. "Kayi haquri captain.....iya na yau ne kawai,dukka masoyane dake daukin dawowarka" Ta amsa masa tana qunshe dariyarta. Shuru ya sakeyi baice komai ba,still cikin kwantar da kai tace. "Ba wani abu daya bayyana,nayi amfani da sutura mafi suturcewa cikin kayan mu na al'ada" Ta fadi tana karyar da wuya. Tasan halinsa.....wani irin farin sani datayi imanin idan bata zama ta uku bayan moti da nanay ba bazata zama ta hudu ba. Bai amsa ba still,saidai ya miqawa akhnan hannunsa,hannun da tabi da kallo a hankali ta aza nata cikin nasa. Dukkaninsu kusan a tare kuma lokaci daya suka sauke wata boyayar ajiyar zuciya. Ba wanda yasan dan uwansa yayi amma Khansaaa ta lura hakan,ta saki siririn murmushi ta koma bayansu ta tsaya. Ta jima tana burin ranar da zataga yadda haisam zai fada soyayya,wala'alla tsohon burinta ne yake dab da cika. A hankali ya kalmashe siraran yatsunta cikin nasa da wani irin yanayi daya tilasta masa lumshe idanunsa,ya fara takawa sai itama ta fara takawa tare dashi suna nufar qofar fita daga jirgin. *zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 08187255862 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 08187255862 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 45* "Na shiga uku!" Aanani dake tsaye kusa da rumaisa cikin wani irin yanayi na bala'in qagauta ci da zuci da jin kamar ta tattaka matakalar jirgin ta qarasa shiga ciki ta taddosu. "Yaa Khansaaa ta dade.....me sukeyi ne a ciki?,don Allah da kalli kusan mintinan mu nawa?......anya ba ramawa yaa Khansaaa zatayi ba?" Maganganun data dinga fadi kenan tana takurawa rumaisa wadda ke cikin Instagram tana duba masu deco din gurin event da Khansaaa tace ta duba musu. "Ya isheni haka mana Aanani?.....idan ba zaki iya jira ba,me zai hana ki shiga ki gayawa Capt obbo din ya dade?" Idanu ta fiddo,ta sani gatsali take mata kawai,don ko giyar wake tasha ina ita ina wannan aikin. "Komai sai kice naje na gani ko na tambaya?.....ba obbo hussam bafa ake magana?,CAPTAIN OBBO nace miki". " Aanani" Rumaisa ta fada wadda maganan Aanani ya tilasta mata sauke ipad din da take kalla ba ta zubewa Aanani din su. "Nayi shuru" Ta fada ganin yadda rumaisa din ta hade rai. Kalmar na shiga ukun data fada ita ta saka rumaisa sakin abinda take ta maida kanta ga Aanani din,saita lura stairs na jirgin take kalla,wannan ya sanyata maida hankalinta gurin cikin takaicin Aanani. Saidai fit duk wani fada data debo zata saukewa Aanani yayi nasa guri. Tasbihi kawai takeyi,wanda tasan yawa yawan mutanen dake gurin suma abinda ke cikin zukatansu da rayukansu. "Man dinnan......ashe yasan wanne tanadi yayi?,ashe ya iya kallon mata?,ashe ya iya zabe ras idanunsa suke?" Rumaisa ta fada tana damqe hannun Aanani,Aananin da nutsuwarta dukka tayi qaura,nata burin kawai su iso gurin,ta rungumi akhnan ta tabbatar da abinda iidanunta suke gani da gaske ne?. Wani irin narkewa kawai zuciyarta keyi cikin wani irin yanayi. Tarbar da suka fara samu tun daga matakalar qarshe cikin kalmomin girmamawar da taji suna fita daga bakin mutanen data tabbatar makusanta ne a gurinsa. Makusantansa ma kenan?,ina ga sauran mutanen gama gari?. Shinfidadden red carpet ne dake dauke da manyan kalmomin welcome cikin wani qasaitaccen rubutun data tabbatar ba daga zaren banza aka saqashi ba,carpet dinne shimfide iyakar ganin da take kyautata zaton tsahonsa yakai har inda zasu qarasa ga motocin da isa da iko yasa aka barsu suka shigo sansanin saukar jiragen daga bangaren da tsaiwarsu bazai bada matsala ba. "English kawai" Khansaaa ke fadiwa su rumaisa tana duban idanunsu. "Duk wanda kika gani anan yana da kusanci dani ta kusa sosai.....qanne....yayye....aunties da uncles dina" Ya fadi qasa qasa da tataccen French dinnan nasa dake sake qone mata ruwan kai da kuma goge mata hadda. Wani abu ta hadiye tana lumshe idanunta,sannan ta gyada masa kanta a hankali. Wani irin sanyi jikinta yakeyi,ya matsa hannunta a hankali yana sake cewa. "Akwai girmamawa sosai a al'adarmu ga dukka wanda ya girmeka,gaisuwa dole ce....a yanzun za'a dauke miki na sani saboda banbancin harshe da yare dake tsakaninmu.....amma zaki san hakaa gaba,zaki koyi hakan....." Ya sake fada softly,daidai sanda Aanani ta gaza jurewa ta tako ta ruskesu. "Ina jin kamar na zama tsuntsuwa na riskeki tun kafin ki fito......barka da zuwa yayarmu" Aanani ta fada tana rungume akhnan Kai tsaye cikin jikinta. Batasan me ya jefa murmushi saman fuskarta ba,amma ta samu kanta da maidawa Aanani martanin rungumartata. "Na gode" Tace da Aanani din,wanda kwarjinin haisam kawai ya sanyata janyewa da baya tana bawa sauran guri. "Muryarta dadi.....wani qamshi takeyi me dadi yaaa rumaisa" Aanani ta fada tana kasa tsaiwa guri daya tsabar zumudi. Tun daga gaisuwar musabaha data fara binsu daya bayan daya sunayi ta soma ganin wani irin kalar karamci. Duk da ba kowa take iya jin abinda yake fada ba,amma yanayin fuskar duk wanda yake gurin tana iya hangen zallar kulawa da girmamawa me tarin yawa a tare da ita. "Saura nan bangaren" Aanani ta fada tana nuna sashen da cousin dinsu maza ke tsaye,saidai ta kasa qarasawa saboda wani kallo da haisam ya aje mata. Daga bayansa ya ajeta,suka qarasa suna gaisawa da masu shekarun ciki. Tana daga bayan nasu take qoqarin gaidasu da harshen English,gaisuwar da bai bari tayi nisa ba ya juya suka soma bin carpet din daya karkata shiyyar da motocinsu ke tsaye suna jira,saidai ko taku uku cikakke basuyi ba wata inuwa ta mamayi saman kansu da wata irin lema ta alfarma,kaman qiftawa da bismillah kuma hadimai suka rufe hagunsu da damansu su da duk wanda yake takawa ta bayansu.....gaba kadan kuma wasu qosassun mutane ne sanye da baqaqen suit da farar 'yar ciki. Komai nasu iri daya ne,hatta da takalman qafarsu kuwa,bata kuma lura dasu ba sai da sukazo dab da inda motocin suka jera kansu. Gaba daya jinin jikinta ne yaso daskarewa na wasu daqiqu,lafiyayyun Rolls Royce ne da adadinsu ya kusa guda goma zalla,sannan wasu BMW din da suka adadinsu ya kusa guda goma din. Biyar daga cikin Rolls Royce din sunfi duk wata mota dake gurin tsada,motocine dake nuna tambari na SARAUTA da masarautar data amsa sunanta wajen cikka izza qasaita da isa. Qirarsu ta daban ce.....sabuwar qirar da sai shekara me zuwa kamfanin zai fiddasu. "Me yasa komai irin wanda jama'a ke jira shekara ta gaba a fitar musu ne?,ya akayi shi yake dasu?" Ta tambayi kanta a rikice idanunta na sauka zuwa qarshen red carpet din. Ddaga inda zai qare kaman qiftawar idanu,ba tare da taga anyi wani motsi na bada umarni ba aka maye gurbin qasar gurin da wani hand Embroidered royal carpet wanda yake bada cultural da royal identity. Wani irin qawataccen zane ne na sarauta.....sarautar gidan ibraheem aba jifar,masarauta mafi girman iko isa da qasaita cikin qasar habasha. Kallon carpet din kawai take tana Takashi a hankali tana qididdige irin kudin da aka zuba wajen saqashi. Wata irin saqar hannu ce dake nuni da zallar iko da isa. A wannan ranar.....bashi ke bude mata qofa ba,kaman yadda bashi yake budewa kansa qofa ba,qofar da kanta tasan da isowarsa,cikin girmamawa kuma akayi wata qaramar magana data zauna da girma sosai a zuciyarta kafin ta bude qofar a hankali. "Welcome sir" Shine abinda qofar kawai ta fadi. Batasan wanne adadin abubuwa take buqata ba kafin ta samu nutsuwar data kamata....shigarta motar sai ya zamana kamar an cireta cak daga wata duniyar ne zuwa wata duniyar ta daban. Ba mota take gani ba itakam,ba wani alamun mota tattare da inda take zaune a yanzu tana kallon yadda hadimai da qwararrun masu tsaron lafiya ke kaffa kaffa dashi cikin wani yanayi na tsantsar qwarewa da tattali,tamkar wata kadara guda daya kenan da suka taba mallaka a rayuwarsu mafi girman daraja da tsada a duniya. "Don Allah kibar motarmu ta bisu.....ban gaji da ganinta ba yaa Khansaaa" "Ba yanzu ba Aanani,ba yanzu ba,baquwace har yanzu batasan komai ba,sannan kin sani ba masarauta za'a wuce da ita kai tsaye ba,al'ada bata bawa kowa da kowa daman ganinta ba,me kikeci na baka na zuba?,taku ce fa,surukar nanay ce" Khansaaa tace da Aanani data so taqi shiga nasu motar da zai maidasu gida. (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) "Amma dai wannan.....an lasa mana zuma ne a baki fa" "Kiyi haquri....karkisa captain yayi magana" Kiran sunan haisam kawai ya sanya Aanani dole ta haqura,ta shiga wata motar daban. Tana jin sanda aka gama busa wani sarewa data tabbatar algaita ce.....amma ba irin algaitarsu sak da sak ba suke ji tsakanin nigeria da niger ba. Wani busa da a kowanne fita da sautin zaiyi GIRMAN IZZA YAKE NUNAWA....suka kammala,convoy na motocin suka soma jera kansu da wani irin tsari da zai gaya maka kowanne driver dake riqe da steering motar tabbas yasan me ake kira mota. Wani shuru ya wanzu cikin motar,shurun daya qara shakka kokwanto da taraddadi me yawa a zuciyarta. Zuciyarta ta qara wani nauyi tare da matsanta mata son sanin amsa guda daya tak da ta nanatawa kanta tambayar WAYESHI har batasan adadi ba. Blue eyes dinta ta daga zuwa gareshi,idanunsa suna kan titi kaman me son gane dame dame qasarsa da yankinsa suka rasa bayan baya nan?. A yau da take kallonsa da shudayen idanunta.....inda ya kula.....inda zai iya daga ido ya kalleta ba abinda zai gane face ROQO DA FATA nason sanin wayeshi da gasken gaske. Saidai a yau din ba zata iya buda bakinta ta tambayeshi kaman yadda ta saba yi a baya ba. Bata kammala wannan tunanin ba taji driver dake jagorancin motar yana isar masa da saqon zasu sauka don tsaiwa su karbi tarba daga shugaban qasa. "Okay" Kawai ya fada da wannan nutsuwar tasa data saukar da wani tasiri a zuciyarta. "Nutsuwa da haiba" Zuciyarta ta fada mata a hankali,abinda ya sanyata dauke kanta zuwa wani sashe na daban tana jin kamar zuciyarta zata narke. Wanne irin duhu yaketa sanyata haka?,me yasa bazai taimaki ruhinta ya taqaita mata wahala da ragaita da tunaninta yakeyi tsakanin tsoro shakka da kokwanto?. Ta daga idanunta a nutse tana maidasu ga window ta cikin baqin gilashin da zai baka daman ganin na waje ba tare da shi ya ganka ba. Shine....mr President na Ethiopia gaba daya Taye atske selassie,tare da prime minister abiy ahmed. Dukkaninsu ta sansu,saboda tafiye tafiye na seminar data tana hadasu a gurare har biyu. "Afwan......khansaa zata kasance da ke,zan sameku a gida in sha Allah......you are safe" Ya fada softly yana bata tabbaci da qwayar idanunsa. Kamata yayi taji bata gamsu ba......kamata yayi taji ta qaryatashi da dukkan ruhinta da gangar jikinta,amma abun takaicin sai taji zuciyarta ba wani d'ar shakka ko kokwanto akan maganarshi. Da idanu ta bishi sanda yake sauka a motar,da dukka nutsuwarsa yake takawa zuwa garesu,ba wani yanayi da zai nuna maka farin shigar haduwa dasu ne,dukkan takunsa da motsinsa yana nuna maka mutumin da aka haifa cikin mulki da iko ne. Idanunta ta janye gabanta na bugawa da qarfin gaske sanda taga yana basu hannu kai tsaye suna musabaha,fuskar nan tasa da madaidaiciyar fara'ar dake qara fidda kyansa da kwarjininsa,daidai sanda khansaa ke shigowa cikin motar. "Sai kinwa angonkin nan uzuri,jama'arsa yawa ne dasu,kowa zai buqaci ganinsa na sani a dawowar nan,zai iya zama busy na wasu lokuta.....amma idan komai ya daidaita....." Saita dakata tana sanin murmushi. "Zaki bada shaidar ba macen data kaiki dacen miji" Ta qarasa fada sanda motar ta fara motsawa a hankali da sauran ayarin motocinsu da suka fita daga cikin nasu prime minister da mr President. *zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 08187255862 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 08187255862 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 46* Sake gyara zamanta hasnaaa tayi,tana gyara lullubin tattausar laffayar jikinta. "Allah yasa kada na dameki.....bana iya zama banyi hirara qanina ba" Ta fada da murmushi. Maganan daya dauke idanun akhnan daga kan hanya,ya maida kan hasnaa irin kallon da baya sauka kai tsaye cikin fuskar mutum. "Ba don yana qanina bane.....amma shi din na dabanne. Inda Allah ya halatta aure tsakanin yaaya da qaninta,inajin da bazan bari ki samu Captain obbo ba" Ta fada da murmushi me sauti. Maganan ya sanya akhnan duban hasnaa kadan,fuskarta da idanuwanta dukka sun nuna mata da gaske take,abinda take fada daga zuciyarta ne. Saita gyada mata kai. "Eh,bani kadai ba,na tabbata dukka qannen haisam idan da zaki tambayesu zasu gaya miki haka.....amma tsaya.....meye sirrin?,wannan zuciyar......ya akayi kika samu muqullin budeta?" Tayi tambayar da sigar tsokana da dariya sosai akan fuskarta. Murmushi kadan akhnan ta saki,haka kawai takejin wani nauyin khansaa ya saukar mata,tayi qasa da idanunta a hankali. Tambayarta bata da amsa.....don bazata iya cewa komai ba. Har yanzu bata sani ba,ita ta saceshi ko shine ya saceta?,a cikin su batasan waye yayi wani aiki gagarumi ba. Kai tsaye ma tana iya cewa aikin na sultane ne.....sultane ne ya shirya komai,ba ita bace......kaman yadda zarginta na farko akan shine silar shirya komai tuni ya tsiyaye tas daga ranta. "Kodai shine ya soma?.....nasan halinsa......yana da wani irin sirri da ban taba ganin gurin kowa ba sai qanina" Ta sake fada tana yin qasa da muryarta da wani salon tsokanar na daban. Yadda take maganan kamar sirri sukeyi yaso bawa akhnan dariya. Wanne irin mutane ne wadannan?,tana hangen izzar sarauta sosai tare dasu da wani irin salo......amma kuma wani sassauqan hali da mu'amala garesu har haka?. Idanunta ta lumshe tana sauraren yadda Khansaa ke bata taqaitattun bayanai akan haisam din. Bayanan data samu kunnuwanta da zurfafa gurin saurararsu,suka kuma dinga buda mata wata siririyar qofa game dashi,saidai qofar batayi fadi ba......bata kuma kaita zuwa inda takeson zuwa kai tsaye ba. "Alhamdulillah mun qaraso" Taji hasnaa tana fadi,daidai sanda wayarta ta dauki qara. Kusan a tare suka maida dubansu kan wayar,ta dago fuskarta fal murmushi. "Nanay ce.....anya nanay zata iya bacci yau?,matar sheikh a jimma kusa da ita?". Ta fadi wani kykkyawan murmushi yana mamaye fuskarta,sannan ta soma qoqarin daga wayar tana barin akhnan da zarcewa duniyar tunani. "Nanay......khansaa.....hasnaaa......obbo......" Komai nasu wani iri yake mata,dukka sunayen baqi ne a kunnenta. Cikakkiyar sallamar data burge akhnan taji hasnaaa din tayi cikin qaramar dariya. "Nanay.....karki damu,matar captain tana cikin aminci......tana tare dani" "Alhamdulillah.......alhamdulillah,karku barta cikin kadaici........abar mata duk wanda takeson kasancewa dashi,idan kun shiga ciki kun kammala komai ki kirani ki hadani da ita". Nanay dake tsaye gaban mirror dinta ta fada tana jin wani sanyi da nutsuwa yana saukar mata. "Da wuri haka nanay?,babu kara ko kadan?" Qaramin murmushi Nanay din ta saki. Komai da takeyi kaara kawai take saboda dattijai dake cikin tafiyar,banda haka.....abinda zatafiso shine,taje da kanta ta tarbo matar muhammad dinta.....ta taka da kanta ta riqo hannunta,ta kaita palace learning residence. Itace mace ta farko da zata fara shiga gidan,wanda an ginashi ne kawai saboda ita. Suruka ta farko ga family din moti ibraheem aba jifar,amma tayi dukkan kawaici ta dauke kai ta barwa masu yi sukayi,hakan bai isa ba?. "Hasnaaa....kiyi yadda yadda nace" "An gama nanay" Ta fada da murmushi tana gimtse kiran,daidai sanda dukkanin motocin suka karkata akalarsu zuwa katafaren gate din me fadi da tsaho. Wata irin qofa Dark carved hardwood me adon gold details,wata irin qofa ce da aka qerata da wani nau'in katako me duhu,katako ke daraja katako ba irin qofar qarfe da aka saba gani ba a dukka main entrance na gidaje. Da wani nau'in gold aka sassaqa zane a jikinta,zanen dake nuna symbol na sarauta da heritage dake nuna qarfin iko. Lokacin da motocin ke qoqarin wucewa ta cikin qofar sai taji kamar sun qanqance saboda fadi da tsahon qofar. Idanunta ta sake saukewa a hankali akan murafun qofar guda biyu,tarihi take tunanawa da al'ada......amma ga duk wanda ya fita a gidan sarauta zai fahimci akwai alfahari wajen sassaqa qofar da kuma narkar da maquden kudade. Zanen zaki ne a jiki,garkuwa da kuma wani irin crown da yasha banban da yanayin wanda ta taba gani. Idanunta ta maida kan mutum biyun da suka bude qofofin don bawa dukkanin motocin damar shigewa. Wasu irin bayi ne manya,masu tsaho kauri da qiba,sama da yadda take ganin girma da cika idanun tamim da kusan yafi kowa cikin masarautar agadez irin wannan qirar. Sanye suke da wasu irin uniform dake nuna cikakakkun ma'aikatan da rayuwarsu ke cikin tsari.....uniform din da zai gaya maka an tsamosu ne daga wata masarauta me cikar izza da iko. Wani irin parking lot ne dake tsare da wasu irin grass carpet na alfarma da wata irin rumfa dake bada yanayin ajiya me kyau,dukkanin motocin,duk yawansu a nan suka samu guri,kafin qofofinsu su fara budewa,saidai tasu motar bataga koda hasnaaa ta bude ba,sai murmushi data sauke mata. "Wannan mutumin....kowa ma sai ya koya masa tsarinsa?,su waye mutanen nan?" Ta tambayi kanta da zuciyarta dake bugawa idanunta suna hangen hadimai da guards da sukayi sahu sahu kamar ba rai a jikinsu tsabar biyayya wa umarnin da bataji wanda yace musu ko kalma daya akan ga yadda zasu tsaya ko kuma ga yadda zasu tsara ba.....tsabar horo.....tsabar iyawa da tsananin qwarewa data zamewa kowanne hadimi ruwan jikinsa sakamakon jagorancin fasihin shugaba yarima me jiran gadon sheikh muhammad haisam. Sai ya zamana kamar kowa yasan kansa,kamar kowa yasan aikinsa.....kamar kowa yasan darajar kansa da muhimmancin lokaci,kamar kowa yasan abinda ya dace yayi a sanda ya dace ba tare da an bata lokacin yin magana da kowa ba. A hankali qofofin motar suka bude da kansu ba tare da kowa ya budesu ba. Wani abu ya tsarga mata tare da sake nauyaya cikin kanta. Ta sani,akwai motocin dake da voice assistance.....akwai masu automatic doors.....amma bata taba tsammaninsu tattare da haisam ba. Ta daya side din hasnaaa ta zagayo,ta miqawa akhnan hannunta tana fadin. "Ki fito da addu'a....Rabbi anzilni munzalan mubarakan wa'anta khairul munzileen.....rabbi adkilni mudkala sidqeen,wa'akhrijni mukhraja sidqeen,waj'alni minladunka suld'anann naseera(addu'o'i ne masu kyau ga amaren da zasu sanya qafafunsu gidajensu na aure,sai a daure kuma a saka niyyar aiki da kykkyawan addu'a da fatan dake cikin ayoyin)". Lokaci daya dukkan ayoyin suka zauna mata a kai,ta maimaitasu kaman yadda taji hasnaaa tayi,sannan ta taimaka mata ta tattare mata rigar don kada ta taketa. Maimakon grass carpet ko interlock ko marbles da take sanya ran gani a qasan,aah....wannan din wani shimfidadden velvet carpet ne me duhu da aka yiwa ado da zaren gold,iyakar ganinta.....ganin daya kai idanunta har hallway din. Babban hallway take iya hanga daga gabansu.....wani irin hallway da aka tsarashi da wasu irin fitilu masu girma da tsaho da suke bada wadataccen hasken daya hana rana fitar da haskenta yadda ya kamata saboda hadarin dake kwance luf cikin sararin samaniyar jimma Ethiopia. (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) A hankali hasnaaa ta saita mata qafafunta zuwa bakin hallway din,ta tsaya cak tana fuskantarsa,daidai sanda siririyar daddadar busar sarewar ta soma tashi,sai tsaiwar ta mata kama irin tsaiwar da wani babban mutum keyi don ayi masa parade na girmamawa. Cikin kintsi da nutsuwa gurin yake,kowa yana tsaye a nutse,yawansu bai sanya komai ya hargitse ba,iya yanayin kawai zai gaya maka harka ce ta mutane masu cike da addini da nutsuwa,wadanda suka samu tarbiyya da horo daga hannun daya dace. Kyakkyawar dattijuwa ce,wankan tarwada dake da matsakaicin tsaho da kuma jiki take takowa ta saman wannan velvet din tana doso akhnan dake tsaye kanta a qasa. Daga bayan matar wasu matasan 'yammata ne guda shida,sanye da tufafi iri daya da suma sukafi kama da tufafin masarauta. Dukkanin su hannayensu dauke suke da wasu irin qawatattun Ornate wooden chests. Kallo daya zaka yiwa abubuwan masu kama da akwati me four corner kasan cewa zallar tarihi da al'ada me nuni da mulki da isa ke tattare dasu,duk kuwa da cewa suna lullube ne da wasu qawatattun yanki deep red silk material Amman hakan bai hana bayyanar qyallinsu ba,da adon gold dake jikin kowannensu. Mutum biyar ne a jere daya a bayan daya cikin Wani irin tsarin da zai nuna maka gogewa da qwarewa gami da sanin makamar aiki ga hadiman. Duk inda aka gifta dasu wani daddadan qamshin turaren amber suke fiddawa dake sake nuna zallar isa da iko. Saman kowanne akwati akai emblem dake nuna kyautar ta musamman ce,ba ordinary kyauta bace. Cikin girmamawa suka qaraso suka kuma rusuna kowanne yana ajiye na hannunsa sannan suka rusuna da wani salon gaisuwa ba tare da sunce komai da ita ba,sannan kuma cikin salon taku suka janye baya daga gabanta. Murmushi dattijuwar tayi,tana matsowa gaban akhnan kadan. Hannunta ta miqa ta kamo hannayen akhnan din ta saka cikin nata. "Muna miki maraba da shigowa ahalin ABA JIFAR.....muna miki maraba da shigowa masarautar Ethiopia jimma......" Wani abu taji me nauyi yana sauka cikin tunaninta da kwanyarta. "Muna miki maraba da shigowa masarautar Ethiopia jimma" Kalmarta ta qarshe data gaza ganeta. Su al'ummar qasar habasha suna yiwa duk wani baqo maraba da shigowa cikin qasar da wannan kalmar ne?,ko tana nufin ita din ta qulla alaqa da wani da yake da mu'amala da masarautar Ethiopia din?. Amsar data maqale cikin iska tana yawo tsakanin kwanyarta da tunaninta,bata kuma samu miqawa sosai ga tunaninta ba sautin matar ya sake katseta. "Wadannan kyaututtuka ne na maraba......." Saita dakata da salon dake nuna mulkin dake jikinta itama. "Domin nuna girmamawa ga matar sheikh dinmu,muhammad haisam.....sannan domin nuna karbuwa da kika samu.......saboda komai da zai fito daga hannun sheikh dinmu yana da daraja kima da martaba me yawan gaske". " Na gode" Ta samu labbanta da maidawa matar da amsa da labbanta da takeji sun mata wani irin nauyi. Abinda takeji baya misaltuwa,a yanxun da suka shiga babban parlor na farko na gidan......tarin mutanen da suke jiran dakon isowarta suka fara miqa kyaututtukansu a gareta cikin wani yanayi na tsananin girma.....wani yanayi na nutsuwa da ba hayaniya,saika dauka duka duka mutanen dake gurin basu haura mutum biyar ba....wani yanayin gabatarwa dake nuna asalin izza da rashin daukan dukiya a wani abu me darajar da za'a kasa kyautar bajinta da ita.....sai takejin kamar wannan gangar jikin bata akhnan bace.....wannan ruhin an musanyashi da wani......wannan ba kyauta bace kawai.....daukaka darajarta kawai akeyi......wannan ba rayuwar zahiri bace gaba daya.....mafarki takeyi. *zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 08187255862 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 08187255862 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 47* Sosai ta narke cikin duvet din tana dora wayar saman kunnenta. Ba zatace ga yanayin data ji ba sanda muryar nan tasa me zurfi take sauka cikin kunnuwanta ba,saidai da qyar ta qwaci kalmomin amsa sallamarsa hotonsa data gama kalla yanzu yana dawo mata cikin kanta. Ta cikin wayar yakejin kamar yana sauraron bugawar zuciyarta,shurun nata yana wani irin qonashi tare da yunqurin binne dukka jarumtarsa. Yana jin kamar da gayya tayi shurun.....kamar tasan abinda yake muradi.... "Me ya samu muryarki haka?" Yayi maganan da wani irin taushi cikin amonsa yana sake jin kamar ana tunzurashi zuwa wancan yanayin. Idanunta ta lumshe,kamar dai dazun muryar na sake shigewa wani gurbi me girma a zuciyarta......kamar ba daga waya yayi maganar ba,kamar gashi gata haka takejin tasirin muryar a cikin jikinta. tana jin yadda yake matsowa kusa da ita sosai,ba da jikinsa ba.......da muryarsa,da wannan yanayin yanayin kulawar tasa da take jin kanta ya kumbura sosai a duk sanda ya nuna mata ita. "Gajiya ce kawai" Ta fada softly da wani yanayi da batasan tayi magana dashi ba. Har cikin qasusuwansa yaji sound din......ya sake matsa recording dinsa yana sauke wata boyayyar ajiyar zuciya. Bai gamsu da maganan data fada ba.....yanayin muryarta kawai akwai wani tasiri me banbancin tsakanin kiran farko da yayi mata da wannan,duk da tsakanin kiran bai dauki lokaci me tsaho ba. "Biftuuu" Ya sake kiranta da sautin daya sanyata taji kaman zata shide. Bata iya amsa masa ba,saboda ta sani,abune me wahala,muryarta ta fita yadda ya kamata,wataqila yaji rauni a muryarta sama da yadda yaji a dazu......wataqila ya gano wani abu da taketa gujewa take avoiding nasa. "Akwai wani abu da baki fadamin ba" Ya fadi da kwantacciyar muryarsa yana jin yadda jikinsa gaba daya yake sake saki. Sosai maganan yazo mata a bazata,ta ware lumsassun idanunta sosai zuciyarta tana bugawa. Akwai nisan tazara a tsakaninsu.....amma me yasa yake iya sansano wani abu?. "Me?" Ta furta a hankali. "Eh" Shima ya bata amsa da wannan husky voice din nasa da kasala ta cikashi fal. Ci gaba da bugawa zuciyarta ta dinga yi,tsoronsa yana cikata. Bata shirya ba sam.....bata shirya karba da fuskantar komai ba a yanzun. Me yasa yake iya gane komai ne?,wanne irin mutum ne shi?. "Me kika boyemin?" Ya tambaya yana cize lips dinsa na qasa saboda tsigar jikinsa data sake tashi sakamakon fitar numfashinta da yaji a hankali ta cikin wayar. Kai ta girgiza da sauri da dukkan qoqarin ta nason binne koma meye takeji a kansa. "Ba komai,me yasa zan boye wani abu?,akwai wani abune a tsakaninmu?" Murmushi me sanyi ya kubce masa wannan karon,murmushin da sautinsa yakai har kunnuwanta ya kuma sake kashe mata jiki gaba daya. Yadda tayi maganan da sauri da salo iri na son kare kai shine abinda ya d'arsa masa wani abu a ranshi,amma a yanzun bayan buqatar jin muryarta so yake hirar tayi tsaho koda kadanne......ya fara samun wani relief yanzu haka. "Eh akwai......akwai biftuuu" Ya furta sunanta a qarshe da wani yanayi dake illata mata zuciya,saita haqura da qoqarin komai ta maida kanta ta sake kwantarwa tana sauke numfashi a hankali. Fargaba takeyi......meye a tsakaninsu?,me ya gano game da ita?,yanayinta ko muryarta?. "Akwai akhnaaan........kewata kike" Ya fadi kai tsaye yana sake fadin sunanta a tausashe. Idanunta ta runtse sosai,kamar wadda taga wani abun tsoro,bugun zuciyarta yana ninkuwa fiye dana dazu. "Waye kai?,don Allah waye kai?" Ta samu kanta da jefa masa tambayar da asalinta adane take a zuciyarta,bata kuma shirya furta masa ita a yanzu ba. Shuru na sakanni,sannan ya saki murmushi kadan. "Wani bawa ne ni......wanda ya sanya bauta a gaba". "Bawa?" "Eh" Ya amsa mata kai tsaye yana son karantar komai daga muryarta. "Bakayi kama da bawa ba" Ta fadi kanta tsaye a wannan karon tana jin takai maqura nason sanin wayeshi. "Bakiyi kama da wadda bata kewata ba......kaman dai na fara cin nasara ko?" Maganarsa ta yanzun ta maida kwadayin son jin amsar tambayar da tayi masa. "Kinji kewata da gaske?" Ya fada muryarsa na sake yin qasa sosai. "Aah" Ta amsa da sauri,saurin da yake sanyashi wani siririn murmushi. A komai tana qoqarin nuna tsayayya ce jajirtacciya ce......saidai a wannan fagen.....a wannan fannin,a wannan bangaren kamar dai bata da wayo. "Shikenan......inzo zaki sake fadi a gaba na?". Idanunta ta soma warewa sosai tana kallon duhun daya mamaye dakin. Inde da gaske zuwan zaiyi a yadda takeji zuciyarta ta narke da kowanne bugu.......a yadda takejin zuciyarta a yau kamar tana shirin fin qarfinta,zuciyarta kamar tana son d'arsa mata wani abu da takejin bai kamata da zuciyarta da rayuwarta ba.......komai zai iya karanta daga idanuwanta,wanda a yanzun sam bata shiryawa hakan ba. Maimakon ta amsa sai kawai ta zabi kashe wayar ta cusata qasan pillow,sannan itama tabi wayar qasan pillow din tana qanqameshi sosai tana kuma jin yadda zuciyarta taci gaba da bugawa. Wayar ya zare daga kunnensa a hankali,wani murmushi da baisan me ya haddasashi saman fuskarsa ba yana subucewa. Ya maida idanunsa saman wayar,yana juyata a hankali a hannunsa. "Wannan shine rauninta" Abinda ya fadi kenan a hankali can qasa maqoshinsa yana motsa labbansa. Yaja iska sosai ta hancinsa yana fitarwa ta bakinsa,yana jin yadda ya samu sassauci sosai,yana kuma jin yadda jikinsa yake sakewa sosai,wata kasala tana baibayeshi. Tunda yake a duniyarshi ba wani sauti ko murya na wata d'iya mace daya taba sanyashi a irin wannan yanayin.......baima tsaya ya saurara ba ballanta ya dasa masa komai cikin kanshi. Amma ita fa?,da sauti kawai?,da dan qaramin kusancin da baiyi zurfin da zai shiga rayuwarsa can ciki ba?,saidai kusancin yana neman masa illa da baisan iyakar inda zai tsaya ba?. "Me yasa?" Ya tambayi kansa sanda ya sauke wata qatotuwar ajiyar zuciya yana jin yadda wankansa ya baci gaba daya. Me yasa qanqanin abu a kanta yake masa tasiri?. Me yasa yakejinta kusa dashi sosai?,bai taba jin irin wannan kusancin ba. Ta tsaya masa a tunaninsa.....itace mace ta farko da zai kalli idanunta yaji wani abu. Itace mace ta farko da zaiji muryarta yaji wani yanayi na daban tattare da shi,itace mace ta farko da zai kalli jikinta yaji tamkar ana fusgarshi. (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) Kiran ahmad muhammad hammud almaz shine ya katse masa tunaninsa,ya shafa wayar yana amsa kiran. Da wannan tarin girmamawar suka gaisa da ahmad,girmamawar da almaz bai banbanceta data mahaifinsa ba. "Bani minti goma zan kiraka yanzun" Yace da ahmad. "To in sha Allah" Ya amsa masa a girmame. Wayar ya katse,sannan ya miqe a nutse ya wuce bathroom,ya tsarkake kansa ya hado da alwala ya dawo,ya tsane jikinsa sosai,wannan gargasar data lullube ko ina na jikinsa. Ya shirya kansa cikin silk Moroccan jubah,fara qal me adon golden din zare. Wani irin kyau yayi.....ajiyayyen kyau da zaka dauka wani ado yayi bawai jallabiyya bace a jikinsa. Ya sani nanay yanzu haka tana can tana jiransa,don haka ya zura flip-flops masu taushi farare ya dauki wayarsa ya soma fita a dakin,qamshinsa yana tsayawa a duk inda ya gifta tamkar bai wuce ba. Kan hanya ya kira ahmad,yana tafiya da nutsuwar nan dake sake nuna kwarjininsa. "Ya yanayin sultane?.....ya komai yake tafiya a masarauta?" Haisam ya fadi yana bada hankalinsa ga ahmad. "Jikinsa yana nan kamar yadda yake......ba wani ci gaba a yanayin farfadowarsa da kuma komawarsa dogon baccinsa". Kai haisam ya gyada a nutse. "Ka nutsu ahmad da kyau......karka karkata damuwarka da sanya idanunka akan ciwon sultane kadai.....a yanzu tarkon da kake ciki yafi wanda sultane yake ciki......ba wanda ya isa ya yiwa sultane komai a yanxu.....kai din kaine abun hari......kaine abu mafi sauqin da za'a cimma,tabaka kawai yana nufin taba ran sultane ne gaba daya" "Bani shawara....." Ahmad ya furta. A duk sanda zaiyi magana da haisam,duk yadda yakai ga sarewa,duk yadda yakai ga mutuwar jiki da rasa fata da buri......maganganun haisam kawai suna gina wannan da gini me qarko a zuciyarsa. Yana gina masa JARUMTA.......yana gina masa YAQINI har sama da yadda yake dashi a baya. "Banason tasan komai......banason tasan rashin lafiyarsa.....duk wanda zai iya gaya mata inaso ka shaida masa abinda nace" "Idan da bamu hadu dakai a rayuwa ba......da yanzun a wanne mataki.muke?" Ahmad ya fada a sanyaye da wani yanayi daya sanya wani irin tausayinsa shida Akhnan samun muhallin zama na sosai cikin zuciyarsa. "Ba azzalumai bane ku,koda babu ni Allah bazai bari ku tozarta ba" Yayi furucin da wani yanayi daya sake sanyawa ahmad nutsuwa me tarin yawa a zuciyarsa. ~Dukkanin magungunan da tasha da allurai bata ji ko guda daya da yayi mata aiki ba. Bata kuma saka ran zaiyi mata aikin,saboda ba maganin daya kamata su bata kenan ba. Ba wanda bai shigo ya mata sannu ba.......ba wanda bai nuna kulawarsa a kanta ba,amma sai takejin wannan kulawar da komai ma sunyi mata kadan. Abinda take gani saman fuskokinsu ke sake daga hankalinta. Kowaccensu daidai da noorah auta cikin walwalarsu suke,walwalat data tabbatar tana da nasaba da isowar matar captain obbo,ta sake tabbatar da hakan kuma sanda ta fito daukan ruwa mara sanyi babban parlour din,ta samesu dukkansu wasu saman sofas wasu zaune a qasa suna sake tattauna maganarta da gagarumar walimar da zasu shirya ranar data fito daga gidan koyon rayuwa da al'adun masarauta. Da qyar ta maida kanta daki,bata kuma sake fitowa daukan ruwan ba sai a yanzu. A daddafe take takawa saboda matsanancin ciwon da kanta yake mata,gabanta ya yanke ya fadi sanda hancinta ya fara jiyo mata wannan qamshin. Shi kadai yake da irin wannan qamshin a duk fadin duniya cikin mutanen data sani......cikin mutanen da take mu'amala dasu. Qamshinsa na dabanne,don haka wanzuwarsa a guri ma ta zama ta daban,kamar yadda koda ya iso guri komai nasa yake banbanta dana kowa. Zataso qafafunta su bata hadin kai tayi gaggawar barin gurin kafin ya iso,amma zuciyarta ta jefawa qafafunta umarnin da har ya iso gurin ta kasa tabuka komai. Bai lura da ita ba,har sai daya kusa shiga dan walkway din da zai sake sadashi da sassan nanay mafi kusanci. "Barka da dare" Ta fada a hankali tana fatan idanunsa yakai kanta tana rusunar da qwayar idanunta qasa. "Yauwa......ya jikin?" Ya fada a tausashe yana dauke idonsa daya sauke a kanta zuwa gabansa. "Alhamdulillah" Sai ya gyada kansa a nutse ya soma takawa zuwa gaba. "Allah ya bada lafiya" Ya fadi a nutse yana sake yin nisa da inda take tsaye. "Ameen" Ta amsa can qasa muryarta tana rawa,tana jin yadda yake qulewa,tana jin yadda yakeyin nisa da inda take tsaye. Duk takunsa saya ruwan hawaye yake saukar mata. Iya abinda zai iyayi kenan?. Me yasa kaman damuwa da lamarinta da kulawar da a baya yake d'an nuna mata sukayi qasa sosai?,me yasa suka ragu fiye da kafin tafiyarsa?. Me yasa bazai karanci damuwarta ba kaman yadda ya saba karantar damuwar 'yan uwansa dama kowa daya damu dashi?,me yasa bazai kalli cikin idanunta ya karanto abinda ke danqare a kansa a zuciyarta ba?. Zuciyarta tayi wani irin rauni,ruwan gorar data dauko ya fara mata nauyi a hannu,ta riqeshi sosai cikin hannun nata,ta daga qafa zata fara takawa maganansa ya mata bazatar data saki ruwan a qasa. "Ko akwai wani ciwon da kikeji?,idan akwai ki fadawa nanay,koda asibiti ne sai a sake da tests ko?" Ya fada da kulawa. Qasa tayi da kanta tana kasa hada idanu dashi,sannan ta daga kanta a hankai. "Da sauqi.....ina samun sauqi" Kai ya jinjina yana sake komawa hanyar walkway din "Ma sha Allah,haka akeso". Tana sake jin yana mata nisa....har zuwa sanda qamshin turarensa ne kawai ya rage a gurin banda wannan gangar jikin da wannan kyakkyawan ruhin da take mafarkin mallaka. Tsugunnawa tayi tana laluben ruwanta daya fadi,saboda hawayen da suka cika mata idanu sun hanata ganinsa,ta aza hannunta akai ta dauka ta miqe da sauri sauri tana wucewa ciki. *zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 08187255862 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 08187255862 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 48* Kuka sosai ta fashe dashi tana qoqarin boye kukanta don kada Aanaani dake zaune tana amsa waya ta jita. Ta lura daidai da kallo ma ba kai tsaye yake kallonta ba. Haka yake kallonsa akan kowacce diya mace yana qoqarin kauda idanunsa a kanki.....amma me yasa sai a yanzun haka yafi zafafarta?. Ta tabbatar ba irin wannan kallon yakewa matarsa ba......bama irin wannan kallon ya mata ba har yaja ra'ayinsa a kanta ba. Me yasa bazai.kalleta da dukkanin idanunsa ba kamar yadda ya kalli matarsa?. Ta tabbatar tana da dukkan wata siffa hali da dabi'a da yakeso game da d'iya mace......ta tabbatar indai zai kalleta yau gobe zuwa jibi.....lallai wataran zata samu kyakkyawan gurbi da muhalli a ransa. Ta sanshi ta karanci dukkan wata dabi'a tasa,tasan abinda yakeso tun daga kan sutura yanayin turare abinci da yanayi(weather)na gari dana muhalli,tayi kuma amfani da dukkan wannan ta fara samar da magana me dan tsaho a tsakaninsu,koda kuwa akan karatu ne amma taci wannan galabar. Ba irin farkon zuwanta ba.....ba kamar a baya ba da daga nesa kurum take hangensa......me zai sanya ta tsaya a iya haka?. "Wacece ita?" Ta samu kanta da tambayar kanta bayan dogon tunanin data gama. A kaf dabi'arsa ta gama gane baya wani ra'ayin mu'amala da mata,baya zurfafa kallo a kansu,wannan ya bata relief na cewa itace kawai zatayi nasarar shiga rayuwarsa. Ta yaya wannan din ta shiga rayuwarsa?,wacece ita?,dame ta fita?,dame take taqama?. Wadannan tambayoyin gaba daya suka kwadaita mata son gani da sanin WACECE AKHNAN. Duk da tana fargaba,zuciyarta kuma tana gaya mata koma wacece zata samu nasarar mallakar sheikh muhammad din tako ina ta cika mace tabbas......to amma kuma tana fata duk cikar da tayi ita ta fita ta kowacce fuska. Tsam nanay ta miqe sanda yake shigowa dakin,fuskarta shimfide da murmushin nan da yake sake nuna dattakonta da tarin nutsuwar da yaranta suka gada daga gareta. Shima nasa idanun suna kanta,yana dubanta da wani kalan tarin qauna da soyayya da tausayi na jiran wasu mutane data dinga yi a rayuwarta na tsahon shekaru ba tare da tana da tabbaci akan komai daya shafesu ba. Ya lumshe idanunsa yana kama hannayenta,yana jin wani irin sassauci da sanyi a ransa a duk sanda ya tuna cewa shine zai zama silar yankewar wannan jiran.....shine zai kusantata da nesanta.....shine zai zame mata tsani na sake rayuwa da mutanen da sukafi soyuwa a ranta. "Zauna nanay" Ya fada yana zaunar da ita saman lallausan tuntum dake zube kan kilishin dake dakin. Bata musa masa ba,ta zauna shima ya dawo gabanta ya zauna saman qafafunsa yana dubanta. "Na dauka kin gaji da jira kin kwanta". Murmushi tayi ta girgiza kai. "Nace zan jiraka muhammad,munyi kewarka sosai.....zanso ace a yanzun haka a irin wannan yanayin surukata tana gefena kamar yadda kake zaune a gabana.....amma al'ada tayi mana wannan shamakin" Ta fada tana murmushi. Yau kawai sai yaji kunyar nanay ta kamashi,yadan sauke kansa qasa. Wai shine da mace?,shine ya auri wata macen?. "Yaya take Muhammad.....gayamin" Da mamaki kadan a fuskarsa ya daga kai yana duban nanay din. Idanunta basu qaryata abinda ya fita yanzu a bakinta ba. Da gaske take tanason ganinta,wacce irin qauna ce wannan?,tun kafin tasan wadda ya kawo mata a matsayin suruka?,tun kafin taga wacece?. Babban abun,a duk lokaci itin wannan da zai dawo daga tafiya ba wanda Nanay takeji ko ta gani saishi,amma a yau maimakon zallar kulawar nan a kansa shi kadai ta soma rabata da wata?. Tun a ranar farko?. "Lafiya alhamdulillah nanay" Kai ta gyada a hankali. "Nace da hasnaaa ta bani ita a dazun muyi magana saita manta.....fatana daya ta kasance me fikira kamar yadda mijinta yake,ta kammala karbar horo cikin qananun kwanaki don ta iso cikin ahali" Qasa yayi da kansa kadan yana murmushi,shi duka ba wannan ba.....izzarta Allah yasa ta barta tayi abinda ya dace,yana fatan izzarta ta barta ta ajiye komai na agadez ta shiga practicing al'adu da dabi'un fada da masarautar aba jifar. "In sha Allah nanay" Ya fada yana zama sosai wannan karon. Hira suka shiga yi a tsakaninsu,irin hirar yaushe gamo. Hirar da take kama da hirar masoyan da sukayi nesa da juna. Abubuwa masu yawa suka tattauna,basa ma ko kallon abincin da tasa aka shirya kala kala daga nau'ikan abinciccikan alfarma na al'adarsu da tasan yafiso. Ya bata labarai kala kala na yadda komai yazo masa. Zuciyarta ta karaya,tayi laushi sosai. Aikinsa a kullum rana tsoro yake sanyata na wanne irin qalubale wataran zai hadu dashi?,amma bata taba yarda ta nuna masa ba. Saboda ta sani,daga ranar daya fahimci abinda yake daga mata hankali,tayi imanin ya ajiye aikin kenan bazai sake waiwayarsa ba duk da yadda yakai ga son aikin. Bata burin ta zama sila ko sanadin hanashi wani jin dadi ko cikar buri na rayuwarsa. Abu daya da take nacewa Allah akai wajen roqa masa shine MACE TA GARI. wadda zata zame masa sanyin idaniya.....wadda zata debe dukkan wani fargaba damuwa da hadari na cikin aikinsa......wadda zata bashi AMINCI ta kuma bashi NUTSUWA. Wadda zata soshi kaman yadda takeson kanta. Wadda zata tare kasa cutarwa.....wadda ba zata bari ya cutu ba tako ina.....uwa uba wadda zata iya dauke dukkan nauyinsa da lalurarsa ta d'a namiji......ta bashi abinda ya kauda kai daga bid'arsa duk da tarin buqatarsa akai.....yayi haquri ya jira halal dinsa. "Nanay" Ya kirata da girmamawa bayan sun kammala cin abincin da ita ta dinga zuba masa har sai daya qoshi. "Sheikh muhammad" Ta fadi da murmushi. Yakanyi murmushi a duk sanda ta kirashi irin hakan,sai yaji sunan kaman yafi dadi a bakinta. "A duniya.....wanne buri ne kike fatan cikarsa kafin ki koma ga mahaliccinki?". Tayi shuru tambayar tana ratsawa cikin kanta. Tana da wasu burika na daban......amma ta sani inde ta riga muhammad rasuwa to zai iya cika mata su,koda bata gani da idanuwanta ba,amma a yanzun burin da take dashi shine taga 'yan uwanta. "Muhammad......burina bana jin me cika ne" Ta fada a raunane. Matsawa gabanta yayi sosai,ya kama hannuwanta ya riqe cikin nasa. "Kija numfashi sosai nanay,ki fadi duk wani burinki,a gaban muhammad dinki kike" Murmushi ya subuce mata dake hade da ruwan hawayen da baikai ga zuba mata ba. "Na sani.....wannan jan gwarzon namijin,zakin d'ana" Maganan ya sashi qaramar dariya,duk da ba yau ya fara jin ta fadi haka a kanshi ba,amma murmushinta kawai ya sanya wani farinciki a zuciyarsa. "Burina naga safiyya da safeena,duk da nasan zai wahala rayuwa ta bamu wannan damar" Ta fadi cikin alamun karaya da yanke tsammani. "Idan na sadaki da koda wani abune daya shafesu......wannan burin naki ya cika?" Samun kanta tayi da qanqame hannunsa sosai har yaji hakan cikin jikinsa,idanunta cikin nasa sosai. "Koda abinda ya shafesu ka hadani dashi muhammad inaji a jikina zai zamana kamar ka hadani dasu ne kai tsaye......amma anya...." "Kisa a ranki a nan kurkusa wannan burin naki zai cika" Har cikin tsakiyar kanta sai da taji wani abu,mamaki ya hanata cewa komai da wata irin shakka data cika zuciyarta. Tafi kowa sani.....ba maqaryaci bane......idan ya fada koda da wasa ne sai ya cika. Wannan ya sanya yake kiyaye harshensa akan fadin abubuwa sosai don baya fadin abinda bazai aikata ba. To amma idan ta gamsu da abinda ya fada fa?. Ta ina zai nemo mutanen da ko burbushinsu ba wanda ya sake gani ko ya sake jin labari shekaru kusan talatin?. Amma kuma gaskiyarsa wata abace da ko yaushe take sake nuna zahirin waye shi. _ki yarda kawai nanay.....mu lu'u lu'u followers muna tayaki murna da haifar jarumi kuma nagartacce,ya rabbi kasa mun haifi sanyin idaniyarmu muma_🙏🏽🙏🏽 ★★★Kwananta daya tak ta soma karbar wasu darussa na sabuwar rayuwar data dinke tunaninta tsaf. Wasu irin al'adu na girmamawa,sutura,yanayin magana da yanayin kula da miji da bata taba ganin irinsu ba. Komai da ake qoqrin azata akai da koya mata mamaki yake bata. Tanason karanta da fahimtar dukka dalilan yin hakan. SARAUTA ta tabbatar gidan wani sarautar ya shigo......gidan sarautar dake da wani irin tsare tsare da tarbiyyar da a tunaninta bata dauka wani gidan sarauta zai kasance irin haka ba. Abu daya da bata gane ba shine......waye shi a masarautar tasu?. A rannan yace mata shi BAWA ne......amma tako ina maganarsa ta gaza shiga zuciyarta da ranta tayi tasiri. Ba wata alama ta bauta a tattare dashi......horon da ake bata kuma baiyi kama da koyarwar da za'a zauna ana yiwa matar bawa ba. Sabuwar rayuwa take shiga......wata irin sabuwar rayuwa da bata taba sanin da zamanta a duniya ba. Sai a sannan ta tuna da zancan aisa. (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) "Duk yadda kike ganin kinsan duniya da yawa,qasashe masu tarin yawa,kin cakuda da mutane qabila kala daban daban......amma akwai inda zaki shiga kiga kin koma kamar wadda batasan komai ba.....rayuwa gaba da gabanta ne.....kafi an fika,Allah ne kawai a sama" Tayi maganan ne tun farko farkon fara zuwan manemanta da sultane ke sahale musu ganinta. Ta raina daya daga cikinsu daya kasance d'an sarkin Cameroon,duk da tarin dukiyarsa da wayewarsa. A lokacin aisa taso ta aureshi......amma ta gaya mata ba'a halicci d'a namijin daya hada dukka qualities din da take buqata daga gurin namiji ba,auren wanda bai hada wadannan nargartar ba tabbas zai zama tozarci ne da qasqanci a tattare da ita,koma baya da rasa martabarta. Wata irin kulawa ake bata.....wata irin girmamawa da tattalin da hatta su birra saida suka raina yadda suke kula da ita a agadez. Komai nata ya canza,daidai da fatarta tasan akwai wani abu daban dake faruwa a rayuwarta. Qamshin jikinta ya zame mata qamshi na biyu dake debe mata kewa bayan qamshinsa.......qamshin turaruka na SHUWA INCENSE AND MORE( +234 704 229 3387) wani qamshi da yake sanyata dadewa cikin duvet duk safiya idan ta farka tana shaqar qamshin yana kai mata har cikin kwanyarta,yana kuma qoqarin kwashe mahaukaciyar kewarsa da takeji tana qoqarin hanata dukkan walwala. Ta dauka a kowacce rana zai shigo ya ganta......ta dauka kowacce rana zata zame masa ta ziyara,saidai abun mamaki babu shi ba dalilinsa. Ba kiransa a cikin kwana biyar din data dauka cikin gidan. Amma a kowacce rana hasnaa da rumaisa da wasu mata da batasan su waye ba suna ziyartar gidan. Cikin kulawa take ta kowacce fuska,cikin kulawa da tattali take da wani irin gata daya sanya ta soma tambayar kanta,wacce irin rayuwa tayi a baya ne?,gata ne da kulawa ta samu?,ko kuma copy ne kawai na gatan ba original ba?. Abun mamakin yadda kwanyarta ke kwashe komai......ita kanta me dora mata tsarin tana ganin mamaki qarara kwance saman fuskarta. Bawai suna da wani qarfin ikon sauya mata rayuwa bane.....aah ta yarda tabi komai yadda aka tsara saboda tana buqatar fita daga gidan. Tana buqatar sanin WAYE SHI?,tana da buqatar ganin anihin rayuwarsa,hakan kuma dukka ba zata samu ba sai tayi qoqarin maida kanta yadda sukeso. *zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 08187255862 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 08187255862 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 49* Suna waya da shehnaz,aisa da morsa lokaci lokaci......amma har yanzu ta gaza samun sultane sai sau daya tak. Shima maganarsu dashi gajeriya ce......ya mata wata magana a qarshe data sanyata fashewa da kuka. "Gida nakeso na dawo bappi......gida nakeso nazo na ganka" Murmushi ya sake mata. "Nace miki ko bayan na mutu kike kuka ko biftu?" Ya fada da murmushi "To ko mutuwa nayi indai haisam bai lamunce kizo ki ganni ba ban yarda kizo ba.....idan kika bishi hakanne zai samawa ruhina salama koda cikin kabarina......duk da ina lafiya cikin qoshin lafiya,muna kan wani aiki ne da yake janyemin lokaci,duk sanda kika nemeni baki sameni ba....karki saka a ranki wani abu ne mara kyau,cikin aminci nake da kiyayewar Allah". Tayita kiran aisa sa shehnaz ko zataji wani abu,amma ba wata alama data nuna akwai damuwa ko matsala cikin masarautar,haka ahmad data kira shima abinda ta gani kenan,wannan ne ya sanya mata nutsuwa a ranta,ta maida hankali ta kammala wancan training din ta fito,tunda duk binciken da tasa a mata sunce basu gano komai a kansa ba,wannan karon ita zata nuna masa adadin nata ikon. Batasan me yake faruwa ba,tasan dai kawai ta tsinci kanta tsundum da yawan duba wayarta. Duk bayan shudewar wasu mintuna saita duba screen din wayarta,daga haka saita fara zarcewa zuwa gurin kira. Takan jima da wayar a kusa da ita,takan jima tana juya wayar a hannunta,batasan me take jira ba,batasan me take nema ba. Sannu a hankali sai wadannan hotunan data fuskanci da yawa an daukesu ba tare daya sani ba......a mabanbantan lokuta a kuma mabanbantan gurare suka zame mata qawaye.....suka zame mata abubuwan da duk rana ranar ba zata fito ta fadi ba bata buda ta kalla ba. Daga qarshe ta sani.....ta bari zuciyarta tayi mummunan sabo da al'amuransa......sabon da batasan meye dalili ba.....sabon da batasan meye ya kawoshi ba......ta sani ta saba ta saba ta saba......amma duk da haka akwai abu daya dataqi yarda a karan kanta cewa SOYAYYA CE. Yarda da cewa tana sonshi tana jin shine qarya ta qarshe da zata qara yarda zuciyarta ta qulla mata. Ta sani tadade da kashe duk wani gurbi na taso wani d'a namiji a zuciyarta. Ko meye takeji ta yarda ta sallama da cewa SABO NE SILA. Tasha kallon number daya kira a wancan ranar......amma kuma ta dade da yiwa zuciyarta bore wadda ke shawartarta ta gwada kiransa. Yasan inda zai ganta......yasan number da zai kira ya sameta,bai nemeta ba......ta yaya dalilin sabo zata bari alfaharinta na diya mace yayi qasa?. Tana tsoron sabo ya karya wannan alfarmar don haka a wani yammaci ta dannawa number delete,amma batasan me ya sanya wani abu ya tsaye mata a wuya ba bayan ta goge number. Ranar farko da hawaye suka cika mata idanu ranar da kewarsa ta hanata bacci. Tayita juyi,tayi alwala tayi sallah duka wannan kewar data rasa wacce iri ce ta hanata sakat. Me yasa duk yadda na dade da sultane da kowa da kowa dake cikin masarauta bana jin girman kewarsu haka a raina?. Me yasa banquntata da yawa ba daga rashinsu a kusa dani?,saishi?.....WAYE SHI?,meye na musamman a tattare dashi da kewarsa ta dara ta kowa nauyi cikin zuciyarta?. D'isar qwallar kawai taji saman cinyarta,sai wani irin mamaki ya kasheta. "Qwalla akhnan?,qwalla saboda kewar D'A NAMIJI?" Ta jima jikinta a sanyaye tana jin zafin abun. Me yasa ta sake masa haka da yawa?,me yasa ta bari suka saba da ganin juna da jin motsin juna?,wanne irin sakarci tayi haka?. Hannu tasa ta dauke qwallar tana gayawa kanta,har yanzu itace dai akhnan muhammad hammud.....bai kamata ta bari wani abu ya karyata ba,amma dai daga qarshe sautinsa.....qira'arsa.....karatun qur'aninsa ta kunna da qaramin sauti can qasa,shine abinda ya sama mata nutsuwar data samu yin bacci a wannan daren. ★★Duk zirga zirgar daya yini cikinta tsakanin gidan prime minister da gidan governor na jimma a yinin ranar data zama ta qarshe tun daga safiya zuwa yanzun da sararin samaniyar jimma ke bada wata lallausar iskar hadari hakan bai ture tunaninta ko sau daya daga ransa ba. Baisan meye me qarfi da girma haka dake maqale da ita a zuciyarsa ba. Kwanaki ne da suka zame masa cikamakin kwanika masu muhimmanci wajen cika alqawari kan aikinsa. Yayi handling muhammad jinjiri ga ahalin ajani a sirrance bisa sharadin ba zasu bayyana dawowarsa cikin ahalin ba har sai ya kammala nasa aikin......ya rufe file na case din mutuwar ajani,ya miqawa gwamnatin qasar Ethiopia tamim babba tamim qarami da dukka qasurgumayen masu laifin da ake ci dasu cikin haramtaccen gidan villa street da ya salwantar dashi. Abu guda daya ya nema su daga masa qafa suyi masa alfarma shine,gurfanar da zaituna cikin asalin qasarta tushenta,wanda ya buqaci su bashi wasu watanni don komai yazo daidai da yadda ya tsara. A yanzun aikin da ya yiwa qasar ba wata alfarma da tafi qarfin ayi masa ita.......bama wannan lokacin ba.....tun a bayan,yana da wani irin girma kima da martabar da gaba yake da alfarma kowacce iri ce,ballantana a yanzun. Ya sake samun wani girman na musamman,darajarsa ta sake ninkuwa,hakanan ya sake shiga cikin abubuwa masu tsada da darajar da qasar Ethiopia din ta mallaka. Ya dauka ya kammala aikin a kwana biyun kawai,saidai ahalin ajani sun dora masa nauyin daya hada da moti na zuwa kebantaccen gurin da moti dinne kawai ya sanshi inda sauran kaso me girma na dukiyar ajani take. Tafiyar tazo masa da wahala sosai,bai sani ba gajiya jikinsa ya fara yi ko kuwa?. Shi kansa ya sani,a wannan karon yayi aikin daya kamata ya daukarwa kansa da kansa hutu,ya bawa gangar jikinsa dama ta huta sosai. Kwanansu uku a gurin suka kammala komai,aka fidda dukiyar data bawa moti lambar yabo daya iya dauke wannan sirri na tsahon shekarun da amininsa ya buqata. Yawan adadin dukiyar daya gigita kowa,saidai moti ya shaida musu,akwai reshe daya daya rage da ajani ya fadawa wani cikin aminansu. Sun zabi killace muhammad a tare dasu,ya saba dasu zuwa sanda haisam zai bada umarnin sadashi da dangin mahaifan safeena kakanninsa kenan. A wannan yammacin da motocin alfarmar da suke zama tambarin prince sheikh muhammad haisam suke tafiya cikin wata irin nutsuwa saman kwaltar......idanunsa can qasa qasa cike da tarin gajiya......idanun da suke zube saman kwalta yana ganin yadda yanayin ya fara juyewa irin yanayin da yakeso......irin yanayin da tsirrai ke wani irin kyau,yanayin da tsirran ke fidda sabbin ganye masu daukan hankali,su kwantar da duk wata qura da ka iya damun dan adam da walwalarsa. Lafiyayyen agogon fatar da yayi luf saman kyakkyawar fatarsa dake lullube da nu'imtacciyar gargasa ya kalla. Yamma tayi sosai.....amma zuciyarsa yaji tana karkata wani guri na daban a maimakon gida. Wani guri ya dan danna daga seat din gabansa (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) "Mu wuce palace training home" Ya furta da wani nutsuwa da jan aji,jan aji da ginshirar data dadu saboda gajiya da kasalar da yakeji. Daga ta cikin abinda ya danna din aka dawo masa da amsa cikin girmamawa,da alama ya tura saqo ne zuwa ga driver din motar. Maida idanunsa yayi kan kwaltar yana kallonta,kafin a hankali murmushi ya subuce masa,wani tattausan murmushi daya qarawa fuskarsa ajiyayyen kyau. Ya sani.....kuma jikinsa yana bashi,zaije ya tarar da wani yanayi tabbas saman fuskarta. Abinda ita kanta bata sani ba.....abinda ya jima shi kuma da kara tarsa da kuma lura dashi shine. Ita din wata iri macace me son kulawa.....macace meson a damu da ita,wanda hakan qila ya samo asali ne daga fake love da fake caring na mammina. Wadda ta kadaita a dukkan komai,ta tattara kulawarta da damuwarta a kanta a zahiri ba tare data hadata komai da kowa ba. Ta tashi da wannan yanayin,ta saba dashi,shi yasa komai yake zuwa mata a baqo a duk sanda aka dauke kai daga lamarinta. Da gaske yayi busy din da dukka wayoyinsa ma basa hannunsa,ya ajiyesu a killataccen guri. Amma behind hakan akwai wani TARKO da yakeso ya d'ana,akwai wani ANALYSIS da yakeso yayi. Daga ranar da hannuwansa suka kai gangar jikinta,daga ranar da hannuwansa sukakai muhalli da guraben da bai taba zaton zasu je ba.....daga ranar ya tabbatar MUTUWA ce kadai zata iya sanyawa ya zare igiyoyin aurenshi daga kanta,koda mutuwar ma baya tunanin ta isa ta sanyashi yayi hakan. Daga ranar daya qetare iyakar da bai taba qetarewa wata mace ba sai a kanta,....daga ranar daya shiga wani yanayi da babu wata diya mace data taba ganinsa a cikin sa,koda kuwa nanay dinsa......daga wannan ranar ya dasawa kansa MALLAKA......ita din mallakinsa ce.....koda da kallo na idanu zaiyi bakin qoqarin hana kowacce halitta isa gareta ta hanyarsa. Yana da kishi......yana da kishi sosai ya sani,wannan kishin bazai taba bari ya barwa wani ita ba. Koda baiji mafi girman soyayya a ransa ba.....amma ya raba wani sirri nasa da ita,ta ganshi cikin wani yanayi na fitar hayyaci,shi kuma bazai taba bawa wani d'a namiji hannuwansa sukai kan inda nashi hannun suka kai ba. Idanunsa ya lumshe yana jin tunaninsa kawai na qarshe kaman an dora masa wuta saman zuciyarsa,sai kawai ya miqa hannu yana sassauta necktie din dake daure a wuyansa cikin lafiyayyar luxury suit din jikinsa da kalarta ta fidda anihin ma'anar kalmar KYAU a tattare dashi,ya maida idanunsa ga hanya sanda suka fada titin da zai sadasu kai tsaye da qofar killataccen gidan. ~Da wannan miskilar fuskartata take zaune birra na qarasa daure mata dogon gashinta a tsakiyar kanta. Fuskarta tayi wani fayau,wani irin ajiyayyen kyau na samun ninkin kulawa da wani sirrantattun abubuwa da batasan amfaninsu ba da suka ratsata. Da farko batasha saboda bai mata kama da abun al'adarta ba,amma daga qarshe zenabu ta zauna ta amintar da ita tasha cikin hikima. Kuma koda tasha din ya mata dadi a baki,ya mata kama da wani abunsha da sukanyi na al'adar buzaye,tun daga ranar bata sake musun sha ba. A girmame aka nemi izinin shigowa sannan aka turo qofar,bata damu ta waiwaya ba,ta zubawa kanta idanu ta ciki madubi tana kallon yadda shigar kayan sukuwar dokin suka mata kyau. Qoqarin kokawa takeyi da tunaninta da dukkanin iyakacin qarfinta......qoqarin koyawa kanta rayuwa takeyi dashi ko ya nemeta ko bai nemeta ba,shi yasa yau da yammar nan ta buqaci a shirya mata doki zata hau cikin gidan tayi sukuwa a faffadan filin wasannin ball dake cikin gidan. Alitash ce,daya daga cikin hadimanta na cikin gidan,wanda sosai takejin dadin zama dasu kamar yadda suke dasu birra. Wasu irin bayi ne data rasa wanne irin horo aka musu haka na iya faranta ran ubangidansu da duk abinda yakeso a sanda ya dace?. Ko a yau da tace tanason hawan dokin,ta dauka a yadda tsare tsarensu yake zasu hana,amma sai gashi tana cikin bathroom tana wanka suka shaida mata an gama shirya komai. Zenabu ce kawai taso tadan mata gyara kan shigar da tayi. Wando ne skinny daya kama jikinta sosai,ya fidda kowanne lungu da saqo da tudu na jikinta,kamar yadda fingilalliyar rigar itama ta fidda dukiyar fulaninta kamar ka saka hannu ka cirosu,suka kuma fidda plate tummy dinta kamar bata taba sanya masa abinci ba tunda Allah ya halicceshi,saidai kuma daga baya ta sanya aka yiwa gurin tsarin da daga ita sai hadiman data zaba su shiga harta gama hawan nata,basu kuma sake cewa komai ba. *zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 08187255862 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 08187255862 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 50* "Allah ya qara daukaka darajarki.....an kammala" Ta fada da girmamawa. Tadan juya ta kalli alitash,sai kawai suka burgeta. "Na gode......" "Amhara tace ko zaki fara cin wani abu?" Alitash ta fada da kulawa. Kai ta gyada a hankali,ba shakka zata iya bawa hadimai da bayin agadez maki casa'in ta cikashewa wadannan zuwa dari bisa dari. Ta fahimci zataje din,saita miqe suna mara mata baya zuwa parlor din da tafi zama cin abinci. Falon yana cikin falukanta da tafiso a 'yan kwanakinta cikin gidan. Komai ya kasance da tsarin gargajiyar dake nuna al'adar oromia. Wasu abubuwan nasu suna burgeta,amma yadda ba wanda yace mata komai,ba wanda ya taba mata bayani,itama bata damu ta daga kanta ta tambaya ba. Kafin ta qaraso sun saita mata takalman da zata sanya ta cire wadanda ta fito dasu a qafarta kamar yadda suka saba,ta zare wadancan ta saka wadanda suka batan,ta fara takawa a nutse tana nufar traditional royal dining table din. Ta san abinda tafi buqata a yammacin,abinci mara nauyi,koda ta makara bataci abincin rana ba,don haka bata takurata da tambayarta me zataci ba,ta soma serving dinta. Wani lafiyayyen farfesu ne me romo sosai data lura akhnan din tana matuqar so cikin irin abinciccikansu. Yana tattare da wani sirri sosai a cikinsa,ta zuba mata oromian black tea daya kasance royal black tea ne saboda tsadar ganyayyakin da ake dafashi dasu,ba gidan kowa kake samunsa ba,kamar yadda ba kasafai ake samunsa ba duk da sune suke nomashi,ta saka mata spoon da fork,sannan dukkaninsu suka tattara suka bar mata parlor din saboda sun karanci bata fiyason cin abinci cikin mutane ba. Tun daga gate din farko da motocinsu suka tsaya aka soma bude dukkanin qofofin gidan da wani iri salo na karramawa da girma. Motocinsa daban suke.....cikin fadin Ethiopia dama qasashen dake maqwabtaka dasu,cikin qanqanin lokaci hadiman dake gidan gaba daya suka zagayeshi cikin marabta ta girma,ya kuma gaisa da kowa cikin mutuntawa da sanin daraja da kimar da Allah ya yiwa dan adam,kafin kowa ya qyaleshi,ya juya ya soma takawa zuwa cikin gidan a nutse. Duk wani setting room ko parlor da zai wuce cikin matuqar girmakawa hadiman dake gurin suke zubewa su gaidashi,sannan kuna su zare jikinsu su fita don sun tabbatar yau yazo ganin gimbiya ne. Baya da dabi'ar son a zube a gaidashi,amma duk yadda yayi dasu sun gaza dainawa. Sunajin ba zasu iya daina gaidashi ta hakan ba,girma da kimarsa da mutuntakar dake tsakaninsu tafi qarfin su iya gaidashi daga tsaye. Kai tsaye ya zarce zuwa parlor din,ya tabbatar tana can,don yana da analysis na motsinta cikin gidan,yana da rahoto kan duk wani abu da tafiso. Wata irin qofa ce da bata bada alama ko sauti ko daya yayin budeta,wannan ya sanya hankali kwance ya janye qofar gefe,ya kuma saka qafarsa a parlor din idanunsa suna dauko masa hotonta a matsayin abu na farko da suka fara gani cikin falon din. Tana zaune saman kujerun,ta dafe gwiwar hannunta dukka biyun da table din. A hankali take juya tea din idanunta cikin cup din,kallo daya zaka mata kasan akwai wani d'an qaramin tunani dake mata kai kawo cikin ranta. Yadda tadan karkatar da kanta ya sanya jelar sumarta da aka fake a tsakiyar kanta ya dawo kafadar hagunta yake reto a hankali daga bayanta zuwa gefan fuskarta. Ta gama juyawa,ta ajiye spoon din a gefe,ta daga mug din ta soma kurba a hankali. Labbanta yabi da kallo,labbanta da hucin ruwan dumin ya sake sanyawa suka sake canza kala.....a idanunsa sunyi looking very soft,abinda ya soma tayar masa da tsumin data dasa masa a dukka gangar jikinsa tun a wancan ranar. Idanunsa ya zame a hankali zuwa santala santalan qafafunta,yayi sama da dubansa har zuwa qugunta daya fito sosai ya bayyana bajajjun mazaunanta da suka dace da shafaffen cikinta. Yadda ta zauna saman kujerar ba'a daidai ba ya sake fidda shape dinta sosai,ya kuma sake fidda fadi da tudun mazaunanta,don ta karkace bangaren damanta ne sosai,sai hakan ya zamana kakar da gayya ta turosu daga daya side din. A hankali yaci gaba da bin sassan jikin nata da kallo,har zuwa sanda ya kawo kan mutanen nasa. Wannan gurin da kallo daya tak ya masa yaji kaman qafafunsa ba zasu iya daukarsa ba......sai kawai ya zube hannuwansa cikin aljihun trouser dinsa ya jingina kafadarsa da jikin qofar,yayi crossing qafafunsa kawai yana ci gaba da narke idanunsa a kansu kamar an bashi aikin kallonta,ko kuma wanda ya shiga gasar iya kallo ta duniya. "Ya salam.....ya salam sallim sallim" Ya furta yana jin yadda ake jona masa wani wiring na shocking cikin jikinsa gaba daya. A cikin jikinta ta soma jin she's not comfortable ba kaman dazu ba,amma sanin cewa ita kadai ce cikin gidan ya sanyata jawo plate din farfesun,ta sanya spoon din,amma ta gaza kaiwa bakinta sai juyawa take a hankali. Ta kusa minti daya kafin takai na farko bakinta,yabi dan qaramin bakinnnata da kallo,yana tuna yanayin daya shiga wancan lokacin daya hade bakunansu guri daya......yana tuna abinda ya dinga ji da yadda kowacce wuta ta jikinsa ta dauke masa. Tana zare spoon din daga bakinta idanunta suna sauka a kansa. Wani bugawa zuciyarta tayi da kyau,bugawar data haddasa mata qwarewa ta ajiye spoon din ta fara tari. Da sauri ya zare hannunsa daga aljihun wandon ya fara takowa sa sassarfa. Kai tsaye ya isa gaban table din,ya dauki gorar ruwan data kasance ruwan kamfanin masarautar ne,ya bude ya tsiyaya mata a cup a gaggauce ya miqa mata. Ta miqa hannunta tana yin tarin a hankali,ga zatonta zai sakar mata cup dinne,amma sai taji ya hada harda hannunta ya riqe gam ya isar da cup din bakinta,sai data fara sha sannan ya zare hannunsa a hankali ya koma da baya a nutse ya zauna saman kujerar dake opposite din tata yana kallonta. Komai nata da jan aji,komai nata akwai isa a ciki,ko yadda takeshan ruwan kawai zakasan akwai ginshira cikin lamarinta. Cire cup din tayi daga bakinta,sannan ta soma ajiyeshi a nutse tana sauke numfashi. Idanunta ta daga ta aza a kansa. Still kallonta yake kaman Allah ya aikoshi,fuskarta ta hade sosai tana jin bugun zuciyarta har yanzu bai daidaita ba. Batason wannan kallon......yana sanyata ta daburce gaba daya.....batason wannan kallon saboda yana karanta mata kai tsaye abinda yake cikin zuciyarta. Bataso ta nuna masa rauninta ko wani abu makamancin haka,don haka ba zata tashi ta bar masa gurin ba,hakanan batasan me zatace dashi ba tunda sai yau ya tuna da ita?,don haka ta sake jawo plate din ta maida spoon din da zummar ci gaba daci,amma kallonsa a kanta yayi yawan data kasa hakan,sai kawai ta zabi ci gaba da juya spoon din. Ya fahimceta duk da batace komai ba,baijin zai iya hana kansa ci gaba da kallonta.....bayajin kuma zai cuci kansa ya janye idanunsa daga kanta,halal ce.....halal dinsa ce.....wannan kallon da yake mata na halal ne......wannan kallon da Allah zai bashi lada ne.....wannan kallon da Allah zai saka ya sake yarda dashi ne,don bai kalli d'iyar kowa ba......bai kalli halalin kowa ba sai nashi. Spoon daya ya zaro shima cikin wani hadadden abu na silver dake gefe wanda aka adana spoons din a cikinsa. Kai tsaye ya zura cikin bata kwanon,ya kuma yi bismillah ya debo ya fara kaiwa cikinsa. Yunwa yakeji.....yunwar da bata tashi ba sai a yanzu da yaga abincin gabanta. Yana lissafe kwanaki daya daya har kwana biyar bai zauna yaci abincin kirki ba,uwa uba kuma ga mura da yakejin alamu tana son kamashi. Duk wannan tunanin duk wannan zaman duk wannan cin naman da yake bai dauke idonsa a kanta ko na second daya ba. Tako ta ina......ta kowanne bangare ya takurata. Kallonsa wani irin dafi yake sauke mata a jikinta wanda ba zata iya jura ba,duk iya yadda take zaton tana da zarrar da zata iya basar masa saita dinga jin kamar idanunsa suna yaye mata kowacce sutura dake jikinta,suturar da wata irin nadamar sakata tazo ta mamayeta,don daidai da bugawar da zuciyarta takeyi ta tabbatar yana iya gani ta d'amammen qirjinta. Batayi qarya ba.....idanunsa suna kai.....idanunsa suna ankare da wajen yana irga adadin bugun zuciyarta daya tabbatar adadin ya zarta yadda ya kamata ya kasance. Can qasan ransa ya saki murmushin da bai nuna a saman fuskarsa ba. Ya sani fushi take,fushin da ya tabbatar koda ya gaya mata dalilin yinsa ba yarda zatayi ba. Idanunta ta maida kan plate din da tun naman farko bata sake kai komai bakinta ba,amma yana dab da cinye naman gaba daya. "To zaman me nake?" Ta tambayi kanta,sai kawai ta ture kujerarta baya da zummar miqewa,saidai kuma kawai taji tattausan tafin hannunsa saman bayan hannunta. Wani irin abu ya tsarga mata yarrrr a jikinta,tana jin wata kewa me nauyi na wannan tattausan tafin hannun tana ratsata,amma a zahiri saita hade rai ta daga blue eyes dinta ta watsa masa. "Zaifi kyau ki zauna mu sasanta a nan your royal highness" Ya fada softly yana sake kasheta da wadannan abubuwan dake cikin narkakkun idanunta. (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) Idanma saqo ya aike mata da gaske ya isa har tsakiyar zuciyarta,taji kaman an ragewa qafafunta qwari,to amma ba zata taba yarda ba. "Me ya faru?,me zamu sasanta?,ba abinda kayimin,kawai zamanka a nan ne banaso,ka tafi" Sune kalaman da takeson gaya masa,amma kamar daukewar ruwa suka dauke daga bakinta,sukaqi bata hadin kai ballantana ta furtasu. Abu daya tayi shine zame hannunta,ta kuma juya ta soma sauka daga gurin,abinda ya bashi full access na ganin komai da komai,da yadda suke juyawa da wani irin yanayi daya fusgi hankalinsa,ya kuma sanya naman tsaiwa saman bakinsa,kafin ya tattara qarfinsa ya hadiyeshi da qyar. Sai kawai ya daina jin duk wani taste na naman,wannan dadin da ya masa ya dauke daga kan harshensa gaba daya,sai ya miqe a nutse yana ture tasa kujerar baya,ya soma takawa da kuzari da burin cinmata sanda take shiga parlour din da daga shi sai bedroom dinta. Tsaiwa tayi tana zare takalman qafarta don musanyasu da bedroom slippers,ta saka qafa daya,tana zura qafa dayar kawai taji an mata wata kyakkyawar runguma daga baya,rungumar data tabbatar duk iya qarfin halinta bata isa ta qwace ba,rungumar data sanyata taji tana narkewa cikin jikinsa gaba daya,shu'umin turarensa yana gaya mata MUHAMMAD HAISAM NE. *NA BIYAKU BASHINKU NA JIYA DAI KO?* *_Assalamu alaikum warahmatullah_* *_Na gode sosai,na gode da jumurinku,duk da na dauka zamu fahimci juna ni daku sama da haka,shi yasa na yita dagewa ina baku pages sama da yadda nake bayarwa,ashe da saura_* *_Ko nawa kake samu a komai ma.....dan adam ne kai akwai gajiya,kana buqatar hutu,ballantana rubutu da yake cinye awanni mafi rinjaye na rayuwarka_* *_kin taba biki na tabbatar,kinsan yadda hidimarsa take,yaushe kika samu kanki sanda kuka fara naki bikin?,yaushe kika gama nutsuwa duka kika koma daidai?_* *_wannan rubutun da kuke ganin muna muku shi,wallahil azeem ko baci ranki yayi a rana bakya iya rubutun,koda kin takura kanki kinyi kowa pages din zasu zowa me karantawa ba armashi,koda yara ne suke gida baka samun nutsuwar yinsa,har sai basa kusa dake,walwala kike buqata,nutsuwa kike buqata ta gaske kafin yin kowanne page_* *_wannan ya sanya sau tari da zaku gane haka don marubuci yayi ALLAH YA ISA ga wanda ke fidda masa pages ba zaku zargeshi ba_* *_shi kadai yasan takura da quncin da yake fuskanta kafin ya hada kowanne page,a haka me sata ya fitar yake zaton ZAICI BULUS A GABAN ALLAH?_* *_Ina amfani da wannan damar na shaida ma masu fidda mana pages ta kowacce hanya cewa,zanta gayawa Allah inde ban taba satar miki komai ba....ban taba cutar miki da komai ba......to Allah ubangijin al'arshi yayi min sakayya Allah ya isana duk wadda ta fitarmin da pages ta kowacce fuska kuwa,Allah ya sakamin_* *_Yadda muka killace haqqinmu kayanmu,kuka watsawa duniya UBANGIJI KA BANKADE SIRRINTA DA TAKE ALKINTAWA A IDANUN DUNIYA,ALLAH KARKA SUTURTATA HAR ABADA_* *_Na gode da jumurin bina da kuke,kuma in sha Allah next time labarinmu zai zamana pages saba'in tamanin kamar yadda aka saba book a baya ayi a qarqareshi_* *zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 08187255862 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 08187255862 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 51 Sosai ta narke cikin duvet din tana dora wayar saman kunnenta. Ba zatace ga yanayin data ji ba sanda muryar nan tasa me zurfi take sauka cikin kunnuwanta ba,saidai da qyar ta qwaci kalmomin amsa sallamarsa hotonsa data gama kalla yanzu yana dawo mata cikin kanta. Ta cikin wayar yakejin kamar yana sauraron bugawar zuciyarta,shurun nata yana wani irin qonashi tare da yunqurin binne dukka jarumtarsa. Yana jin kamar da gayya tayi shurun.....kamar tasan abinda yake muradi.... "Me ya samu muryarki haka?" Yayi maganan da wani irin taushi cikin amonsa yana sake jin kamar ana tunzurashi zuwa wancan yanayin. Idanunta ta lumshe,kamar dai dazun muryar na sake shigewa wani gurbi me girma a zuciyarta......kamar ba daga waya yayi maganar ba,kamar gashi gata haka takejin tasirin muryar a cikin jikinta. tana jin yadda yake matsowa kusa da ita sosai,ba da jikinsa ba.......da muryarsa,da wannan yanayin yanayin kulawar tasa da take jin kanta ya kumbura sosai a duk sanda ya nuna mata ita. "Gajiya ce kawai" Ta fada softly da wani yanayi da batasan tayi magana dashi ba. Har cikin qasusuwansa yaji sound din......ya sake matsa recording dinsa yana sauke wata boyayyar ajiyar zuciya. Bai gamsu da maganan data fada ba.....yanayin muryarta kawai akwai wani tasiri me banbancin tsakanin kiran farko da yayi mata da wannan,duk da tsakanin kiran bai dauki lokaci me tsaho ba. "Biftuuu" Ya sake kiranta da sautin daya sanyata taji kaman zata shide. Bata iya amsa masa ba,saboda ta sani,abune me wahala,muryarta ta fita yadda ya kamata,wataqila yaji rauni a muryarta sama da yadda yaji a dazu......wataqila ya gano wani abu da taketa gujewa take avoiding nasa. "Akwai wani abu da baki fadamin ba" Ya fadi da kwantacciyar muryarsa yana jin yadda jikinsa gaba daya yake sake saki. Sosai maganan yazo mata a bazata,ta ware lumsassun idanunta sosai zuciyarta tana bugawa. Akwai nisan tazara a tsakaninsu.....amma me yasa yake iya sansano wani abu?. "Me?" Ta furta a hankali. "Eh" Shima ya bata amsa da wannan husky voice din nasa da kasala ta cikashi fal. Ci gaba da bugawa zuciyarta ta dinga yi,tsoronsa yana cikata. Bata shirya ba sam.....bata shirya karba da fuskantar komai ba a yanzun. Me yasa yake iya gane komai ne?,wanne irin mutum ne shi?. "Me kika boyemin?" Ya tambaya yana cize lips dinsa na qasa saboda tsigar jikinsa data sake tashi sakamakon fitar numfashinta da yaji a hankali ta cikin wayar. Kai ta girgiza da sauri da dukkan qoqarin ta nason binne koma meye takeji a kansa. "Ba komai,me yasa zan boye wani abu?,akwai wani abune a tsakaninmu?" Murmushi me sanyi ya kubce masa wannan karon,murmushin da sautinsa yakai har kunnuwanta ya kuma sake kashe mata jiki gaba daya. Yadda tayi maganan da sauri da salo iri na son kare kai shine abinda ya d'arsa masa wani abu a ranshi,amma a yanzun bayan buqatar jin muryarta so yake hirar tayi tsaho koda kadanne......ya fara samun wani relief yanzu haka. "Eh akwai......akwai biftuuu" Ya furta sunanta a qarshe da wani yanayi dake illata mata zuciya,saita haqura da qoqarin komai ta maida kanta ta sake kwantarwa tana sauke numfashi a hankali. Fargaba takeyi......meye a tsakaninsu?,me ya gano game da ita?,yanayinta ko muryarta?. "Akwai akhnaaan........kewata kike" Ya fadi kai tsaye yana sake fadin sunanta a tausashe. Idanunta ta runtse sosai,kamar wadda taga wani abun tsoro,bugun zuciyarta yana ninkuwa fiye dana dazu. "Waye kai?,don Allah waye kai?" Ta samu kanta da jefa masa tambayar da asalinta adane take a zuciyarta,bata kuma shirya furta masa ita a yanzu ba. Shuru na sakanni,sannan ya saki murmushi kadan. "Wani bawa ne ni......wanda ya sanya bauta a gaba". "Bawa?" "Eh" Ya amsa mata kai tsaye yana son karantar komai daga muryarta. "Bakayi kama da bawa ba" Ta fadi kanta tsaye a wannan karon tana jin takai maqura nason sanin wayeshi. "Bakiyi kama da wadda bata kewata ba......kaman dai na fara cin nasara ko?" Maganarsa ta yanzun ta maida kwadayin son jin amsar tambayar da tayi masa. "Kinji kewata da gaske?" Ya fada muryarsa na sake yin qasa sosai. "Aah" Ta amsa da sauri,saurin da yake sanyashi wani siririn murmushi. A komai tana qoqarin nuna tsayayya ce jajirtacciya ce......saidai a wannan fagen.....a wannan fannin,a wannan bangaren kamar dai bata da wayo. "Shikenan......inzo zaki sake fadi a gaba na?". Idanunta ta soma warewa sosai tana kallon duhun daya mamaye dakin. Inde da gaske zuwan zaiyi a yadda takeji zuciyarta ta narke da kowanne bugu.......a yadda takejin zuciyarta a yau kamar tana shirin fin qarfinta,zuciyarta kamar tana son d'arsa mata wani abu da takejin bai kamata da zuciyarta da rayuwarta ba.......komai zai iya karanta daga idanuwanta,wanda a yanzun sam bata shiryawa hakan ba. Maimakon ta amsa sai kawai ta zabi kashe wayar ta cusata qasan pillow,sannan itama tabi wayar qasan pillow din tana qanqameshi sosai tana kuma jin yadda zuciyarta taci gaba da bugawa. Wayar ya zare daga kunnensa a hankali,wani murmushi da baisan me ya haddasashi saman fuskarsa ba yana subucewa. Ya maida idanunsa saman wayar,yana juyata a hankali a hannunsa. "Wannan shine rauninta" Abinda ya fadi kenan a hankali can qasa maqoshinsa yana motsa labbansa. Yaja iska sosai ta hancinsa yana fitarwa ta bakinsa,yana jin yadda ya samu sassauci sosai,yana kuma jin yadda jikinsa yake sakewa sosai,wata kasala tana baibayeshi. Tunda yake a duniyarshi ba wani sauti ko murya na wata d'iya mace daya taba sanyashi a irin wannan yanayin.......baima tsaya ya saurara ba ballanta ya dasa masa komai cikin kanshi. Amma ita fa?,da sauti kawai?,da dan qaramin kusancin da baiyi zurfin da zai shiga rayuwarsa can ciki ba?,saidai kusancin yana neman masa illa da baisan iyakar inda zai tsaya ba?. "Me yasa?" Ya tambayi kansa sanda ya sauke wata qatotuwar ajiyar zuciya yana jin yadda wankansa ya baci gaba daya. Me yasa qanqanin abu a kanta yake masa tasiri?. Me yasa yakejinta kusa dashi sosai?,bai taba jin irin wannan kusancin ba. Ta tsaya masa a tunaninsa.....itace mace ta farko da zai kalli idanunta yaji wani abu. Itace mace ta farko da zaiji muryarta yaji wani yanayi na daban tattare da shi,itace mace ta farko da zai kalli jikinta yaji tamkar ana fusgarshi. (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) Kiran ahmad muhammad hammud almaz shine ya katse masa tunaninsa,ya shafa wayar yana amsa kiran. Da wannan tarin girmamawar suka gaisa da ahmad,girmamawar da almaz bai banbanceta data mahaifinsa ba. "Bani minti goma zan kiraka yanzun" Yace da ahmad. "To in sha Allah" Ya amsa masa a girmame. Wayar ya katse,sannan ya miqe a nutse ya wuce bathroom,ya tsarkake kansa ya hado da alwala ya dawo,ya tsane jikinsa sosai,wannan gargasar data lullube ko ina na jikinsa. Ya shirya kansa cikin silk Moroccan jubah,fara qal me adon golden din zare. Wani irin kyau yayi.....ajiyayyen kyau da zaka dauka wani ado yayi bawai jallabiyya bace a jikinsa. Ya sani nanay yanzu haka tana can tana jiransa,don haka ya zura flip-flops masu taushi farare ya dauki wayarsa ya soma fita a dakin,qamshinsa yana tsayawa a duk inda ya gifta tamkar bai wuce ba. Kan hanya ya kira ahmad,yana tafiya da nutsuwar nan dake sake nuna kwarjininsa. "Ya yanayin sultane?.....ya komai yake tafiya a masarauta?" Haisam ya fadi yana bada hankalinsa ga ahmad. "Jikinsa yana nan kamar yadda yake......ba wani ci gaba a yanayin farfadowarsa da kuma komawarsa dogon baccinsa". Kai haisam ya gyada a nutse. "Ka nutsu ahmad da kyau......karka karkata damuwarka da sanya idanunka akan ciwon sultane kadai.....a yanzu tarkon da kake ciki yafi wanda sultane yake ciki......ba wanda ya isa ya yiwa sultane komai a yanxu.....kai din kaine abun hari......kaine abu mafi sauqin da za'a cimma,tabaka kawai yana nufin taba ran sultane ne gaba daya" "Bani shawara....." Ahmad ya furta. A duk sanda zaiyi magana da haisam,duk yadda yakai ga sarewa,duk yadda yakai ga mutuwar jiki da rasa fata da buri......maganganun haisam kawai suna gina wannan da gini me qarko a zuciyarsa. Yana gina masa JARUMTA.......yana gina masa YAQINI har sama da yadda yake dashi a baya. "Banason tasan komai......banason tasan rashin lafiyarsa.....duk wanda zai iya gaya mata inaso ka shaida masa abinda nace" "Idan da bamu hadu dakai a rayuwa ba......da yanzun a wanne mataki.muke?" Ahmad ya fada a sanyaye da wani yanayi daya sanya wani irin tausayinsa shida Akhnan samun muhallin zama na sosai cikin zuciyarsa. "Ba azzalumai bane ku,koda babu ni Allah bazai bari ku tozarta ba" Yayi furucin da wani yanayi daya sake sanyawa ahmad nutsuwa me tarin yawa a zuciyarsa. ~Dukkanin magungunan da tasha da allurai bata ji ko guda daya da yayi mata aiki ba. Bata kuma saka ran zaiyi mata aikin,saboda ba maganin daya kamata su bata kenan ba. Ba wanda bai shigo ya mata sannu ba.......ba wanda bai nuna kulawarsa a kanta ba,amma sai takejin wannan kulawar da komai ma sunyi mata kadan. Abinda take gani saman fuskokinsu ke sake daga hankalinta. Kowaccensu daidai da noorah auta cikin walwalarsu suke,walwalat data tabbatar tana da nasaba da isowar matar captain obbo,ta sake tabbatar da hakan kuma sanda ta fito daukan ruwa mara sanyi babban parlour din,ta samesu dukkansu wasu saman sofas wasu zaune a qasa suna sake tattauna maganarta da gagarumar walimar da zasu shirya ranar data fito daga gidan koyon rayuwa da al'adun masarauta. Da qyar ta maida kanta daki,bata kuma sake fitowa daukan ruwan ba sai a yanzu. A daddafe take takawa saboda matsanancin ciwon da kanta yake mata,gabanta ya yanke ya fadi sanda hancinta ya fara jiyo mata wannan qamshin. Shi kadai yake da irin wannan qamshin a duk fadin duniya cikin mutanen data sani......cikin mutanen da take mu'amala dasu. Qamshinsa na dabanne,don haka wanzuwarsa a guri ma ta zama ta daban,kamar yadda koda ya iso guri komai nasa yake banbanta dana kowa. Zataso qafafunta su bata hadin kai tayi gaggawar barin gurin kafin ya iso,amma zuciyarta ta jefawa qafafunta umarnin da har ya iso gurin ta kasa tabuka komai. Bai lura da ita ba,har sai daya kusa shiga dan walkway din da zai sake sadashi da sassan nanay mafi kusanci. "Barka da dare" Ta fada a hankali tana fatan idanunsa yakai kanta tana rusunar da qwayar idanunta qasa. "Yauwa......ya jikin?" Ya fada a tausashe yana dauke idonsa daya sauke a kanta zuwa gabansa. "Alhamdulillah" Sai ya gyada kansa a nutse ya soma takawa zuwa gaba. "Allah ya bada lafiya" Ya fadi a nutse yana sake yin nisa da inda take tsaye. "Ameen" Ta amsa can qasa muryarta tana rawa,tana jin yadda yake qulewa,tana jin yadda yakeyin nisa da inda take tsaye. Duk takunsa saya ruwan hawaye yake saukar mata. Iya abinda zai iyayi kenan?. Me yasa kaman damuwa da lamarinta da kulawar da a baya yake d'an nuna mata sukayi qasa sosai?,me yasa suka ragu fiye da kafin tafiyarsa?. Me yasa bazai karanci damuwarta ba kaman yadda ya saba karantar damuwar 'yan uwansa dama kowa daya damu dashi?,me yasa bazai kalli cikin idanunta ya karanto abinda ke danqare a kansa a zuciyarta ba?. Zuciyarta tayi wani irin rauni,ruwan gorar data dauko ya fara mata nauyi a hannu,ta riqeshi sosai cikin hannun nata,ta daga qafa zata fara takawa maganansa ya mata bazatar data saki ruwan a qasa. "Ko akwai wani ciwon da kikeji?,idan akwai ki fadawa nanay,koda asibiti ne sai a sake da tests ko?" Ya fada da kulawa. Qasa tayi da kanta tana kasa hada idanu dashi,sannan ta daga kanta a hankai. "Da sauqi.....ina samun sauqi" Kai ya jinjina yana sake komawa hanyar walkway din "Ma sha Allah,haka akeso". Tana sake jin yana mata nisa....har zuwa sanda qamshin turarensa ne kawai ya rage a gurin banda wannan gangar jikin da wannan kyakkyawan ruhin da take mafarkin mallaka. Tsugunnawa tayi tana laluben ruwanta daya fadi,saboda hawayen da suka cika mata idanu sun hanata ganinsa,ta aza hannunta akai ta dauka ta miqe da sauri sauri tana wucewa ciki. *zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 08187255862 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 08187255862 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 52 Kuka sosai ta fashe dashi tana qoqarin boye kukanta don kada Aanaani dake zaune tana amsa waya ta jita. Ta lura daidai da kallo ma ba kai tsaye yake kallonta ba. Haka yake kallonsa akan kowacce diya mace yana qoqarin kauda idanunsa a kanki.....amma me yasa sai a yanzun haka yafi zafafarta?. Ta tabbatar ba irin wannan kallon yakewa matarsa ba......bama irin wannan kallon ya mata ba har yaja ra'ayinsa a kanta ba. Me yasa bazai.kalleta da dukkanin idanunsa ba kamar yadda ya kalli matarsa?. Ta tabbatar tana da dukkan wata siffa hali da dabi'a da yakeso game da d'iya mace......ta tabbatar indai zai kalleta yau gobe zuwa jibi.....lallai wataran zata samu kyakkyawan gurbi da muhalli a ransa. Ta sanshi ta karanci dukkan wata dabi'a tasa,tasan abinda yakeso tun daga kan sutura yanayin turare abinci da yanayi(weather)na gari dana muhalli,tayi kuma amfani da dukkan wannan ta fara samar da magana me dan tsaho a tsakaninsu,koda kuwa akan karatu ne amma taci wannan galabar. Ba irin farkon zuwanta ba.....ba kamar a baya ba da daga nesa kurum take hangensa......me zai sanya ta tsaya a iya haka?. "Wacece ita?" Ta samu kanta da tambayar kanta bayan dogon tunanin data gama. A kaf dabi'arsa ta gama gane baya wani ra'ayin mu'amala da mata,baya zurfafa kallo a kansu,wannan ya bata relief na cewa itace kawai zatayi nasarar shiga rayuwarsa. Ta yaya wannan din ta shiga rayuwarsa?,wacece ita?,dame ta fita?,dame take taqama?. Wadannan tambayoyin gaba daya suka kwadaita mata son gani da sanin WACECE AKHNAN. Duk da tana fargaba,zuciyarta kuma tana gaya mata koma wacece zata samu nasarar mallakar sheikh muhammad din tako ina ta cika mace tabbas......to amma kuma tana fata duk cikar da tayi ita ta fita ta kowacce fuska. Tsam nanay ta miqe sanda yake shigowa dakin,fuskarta shimfide da murmushin nan da yake sake nuna dattakonta da tarin nutsuwar da yaranta suka gada daga gareta. Shima nasa idanun suna kanta,yana dubanta da wani kalan tarin qauna da soyayya da tausayi na jiran wasu mutane data dinga yi a rayuwarta na tsahon shekaru ba tare da tana da tabbaci akan komai daya shafesu ba. Ya lumshe idanunsa yana kama hannayenta,yana jin wani irin sassauci da sanyi a ransa a duk sanda ya tuna cewa shine zai zama silar yankewar wannan jiran.....shine zai kusantata da nesanta.....shine zai zame mata tsani na sake rayuwa da mutanen da sukafi soyuwa a ranta. "Zauna nanay" Ya fada yana zaunar da ita saman lallausan tuntum dake zube kan kilishin dake dakin. Bata musa masa ba,ta zauna shima ya dawo gabanta ya zauna saman qafafunsa yana dubanta. "Na dauka kin gaji da jira kin kwanta". Murmushi tayi ta girgiza kai. "Nace zan jiraka muhammad,munyi kewarka sosai.....zanso ace a yanzun haka a irin wannan yanayin surukata tana gefena kamar yadda kake zaune a gabana.....amma al'ada tayi mana wannan shamakin" Ta fada tana murmushi. Yau kawai sai yaji kunyar nanay ta kamashi,yadan sauke kansa qasa. Wai shine da mace?,shine ya auri wata macen?. "Yaya take Muhammad.....gayamin" Da mamaki kadan a fuskarsa ya daga kai yana duban nanay din. Idanunta basu qaryata abinda ya fita yanzu a bakinta ba. Da gaske take tanason ganinta,wacce irin qauna ce wannan?,tun kafin tasan wadda ya kawo mata a matsayin suruka?,tun kafin taga wacece?. Babban abun,a duk lokaci itin wannan da zai dawo daga tafiya ba wanda Nanay takeji ko ta gani saishi,amma a yau maimakon zallar kulawar nan a kansa shi kadai ta soma rabata da wata?. Tun a ranar farko?. "Lafiya alhamdulillah nanay" Kai ta gyada a hankali. "Nace da hasnaaa ta bani ita a dazun muyi magana saita manta.....fatana daya ta kasance me fikira kamar yadda mijinta yake,ta kammala karbar horo cikin qananun kwanaki don ta iso cikin ahali" Qasa yayi da kansa kadan yana murmushi,shi duka ba wannan ba.....izzarta Allah yasa ta barta tayi abinda ya dace,yana fatan izzarta ta barta ta ajiye komai na agadez ta shiga practicing al'adu da dabi'un fada da masarautar aba jifar. "In sha Allah nanay" Ya fada yana zama sosai wannan karon. Hira suka shiga yi a tsakaninsu,irin hirar yaushe gamo. Hirar da take kama da hirar masoyan da sukayi nesa da juna. Abubuwa masu yawa suka tattauna,basa ma ko kallon abincin da tasa aka shirya kala kala daga nau'ikan abinciccikan alfarma na al'adarsu da tasan yafiso. Ya bata labarai kala kala na yadda komai yazo masa. Zuciyarta ta karaya,tayi laushi sosai. Aikinsa a kullum rana tsoro yake sanyata na wanne irin qalubale wataran zai hadu dashi?,amma bata taba yarda ta nuna masa ba. Saboda ta sani,daga ranar daya fahimci abinda yake daga mata hankali,tayi imanin ya ajiye aikin kenan bazai sake waiwayarsa ba duk da yadda yakai ga son aikin. Bata burin ta zama sila ko sanadin hanashi wani jin dadi ko cikar buri na rayuwarsa. Abu daya da take nacewa Allah akai wajen roqa masa shine MACE TA GARI. wadda zata zame masa sanyin idaniya.....wadda zata debe dukkan wani fargaba damuwa da hadari na cikin aikinsa......wadda zata bashi AMINCI ta kuma bashi NUTSUWA. Wadda zata soshi kaman yadda takeson kanta. Wadda zata tare kasa cutarwa.....wadda ba zata bari ya cutu ba tako ina.....uwa uba wadda zata iya dauke dukkan nauyinsa da lalurarsa ta d'a namiji......ta bashi abinda ya kauda kai daga bid'arsa duk da tarin buqatarsa akai.....yayi haquri ya jira halal dinsa. "Nanay" Ya kirata da girmamawa bayan sun kammala cin abincin da ita ta dinga zuba masa har sai daya qoshi. "Sheikh muhammad" Ta fadi da murmushi. Yakanyi murmushi a duk sanda ta kirashi irin hakan,sai yaji sunan kaman yafi dadi a bakinta. "A duniya.....wanne buri ne kike fatan cikarsa kafin ki koma ga mahaliccinki?". Tayi shuru tambayar tana ratsawa cikin kanta. Tana da wasu burika na daban......amma ta sani inde ta riga muhammad rasuwa to zai iya cika mata su,koda bata gani da idanuwanta ba,amma a yanzun burin da take dashi shine taga 'yan uwanta. "Muhammad......burina bana jin me cika ne" Ta fada a raunane. Matsawa gabanta yayi sosai,ya kama hannuwanta ya riqe cikin nasa. "Kija numfashi sosai nanay,ki fadi duk wani burinki,a gaban muhammad dinki kike" Murmushi ya subuce mata dake hade da ruwan hawayen da baikai ga zuba mata ba. "Na sani.....wannan jan gwarzon namijin,zakin d'ana" Maganan ya sashi qaramar dariya,duk da ba yau ya fara jin ta fadi haka a kanshi ba,amma murmushinta kawai ya sanya wani farinciki a zuciyarsa. "Burina naga safiyya da safeena,duk da nasan zai wahala rayuwa ta bamu wannan damar" Ta fadi cikin alamun karaya da yanke tsammani. "Idan na sadaki da koda wani abune daya shafesu......wannan burin naki ya cika?" Samun kanta tayi da qanqame hannunsa sosai har yaji hakan cikin jikinsa,idanunta cikin nasa sosai. "Koda abinda ya shafesu ka hadani dashi muhammad inaji a jikina zai zamana kamar ka hadani dasu ne kai tsaye......amma anya...." "Kisa a ranki a nan kurkusa wannan burin naki zai cika" Har cikin tsakiyar kanta sai da taji wani abu,mamaki ya hanata cewa komai da wata irin shakka data cika zuciyarta. Tafi kowa sani.....ba maqaryaci bane......idan ya fada koda da wasa ne sai ya cika. Wannan ya sanya yake kiyaye harshensa akan fadin abubuwa sosai don baya fadin abinda bazai aikata ba. To amma idan ta gamsu da abinda ya fada fa?. Ta ina zai nemo mutanen da ko burbushinsu ba wanda ya sake gani ko ya sake jin labari shekaru kusan talatin?. Amma kuma gaskiyarsa wata abace da ko yaushe take sake nuna zahirin waye shi. _ki yarda kawai nanay.....mu lu'u lu'u followers muna tayaki murna da haifar jarumi kuma nagartacce,ya rabbi kasa mun haifi sanyin idaniyarmu muma_🙏🏽🙏🏽 ★★★Kwananta daya tak ta soma karbar wasu darussa na sabuwar rayuwar data dinke tunaninta tsaf. Wasu irin al'adu na girmamawa,sutura,yanayin magana da yanayin kula da miji da bata taba ganin irinsu ba. Komai da ake qoqrin azata akai da koya mata mamaki yake bata. Tanason karanta da fahimtar dukka dalilan yin hakan. SARAUTA ta tabbatar gidan wani sarautar ya shigo......gidan sarautar dake da wani irin tsare tsare da tarbiyyar da a tunaninta bata dauka wani gidan sarauta zai kasance irin haka ba. Abu daya da bata gane ba shine......waye shi a masarautar tasu?. A rannan yace mata shi BAWA ne......amma tako ina maganarsa ta gaza shiga zuciyarta da ranta tayi tasiri. Ba wata alama ta bauta a tattare dashi......horon da ake bata kuma baiyi kama da koyarwar da za'a zauna ana yiwa matar bawa ba. Sabuwar rayuwa take shiga......wata irin sabuwar rayuwa da bata taba sanin da zamanta a duniya ba. Sai a sannan ta tuna da zancan aisa. (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) "Duk yadda kike ganin kinsan duniya da yawa,qasashe masu tarin yawa,kin cakuda da mutane qabila kala daban daban......amma akwai inda zaki shiga kiga kin koma kamar wadda batasan komai ba.....rayuwa gaba da gabanta ne.....kafi an fika,Allah ne kawai a sama" Tayi maganan ne tun farko farkon fara zuwan manemanta da sultane ke sahale musu ganinta. Ta raina daya daga cikinsu daya kasance d'an sarkin Cameroon,duk da tarin dukiyarsa da wayewarsa. A lokacin aisa taso ta aureshi......amma ta gaya mata ba'a halicci d'a namijin daya hada dukka qualities din da take buqata daga gurin namiji ba,auren wanda bai hada wadannan nargartar ba tabbas zai zama tozarci ne da qasqanci a tattare da ita,koma baya da rasa martabarta. Wata irin kulawa ake bata.....wata irin girmamawa da tattalin da hatta su birra saida suka raina yadda suke kula da ita a agadez. Komai nata ya canza,daidai da fatarta tasan akwai wani abu daban dake faruwa a rayuwarta. Qamshin jikinta ya zame mata qamshi na biyu dake debe mata kewa bayan qamshinsa.......qamshin turaruka na SHUWA INCENSE AND MORE( +234 704 229 3387) wani qamshi da yake sanyata dadewa cikin duvet duk safiya idan ta farka tana shaqar qamshin yana kai mata har cikin kwanyarta,yana kuma qoqarin kwashe mahaukaciyar kewarsa da takeji tana qoqarin hanata dukkan walwala. Ta dauka a kowacce rana zai shigo ya ganta......ta dauka kowacce rana zata zame masa ta ziyara,saidai abun mamaki babu shi ba dalilinsa. Ba kiransa a cikin kwana biyar din data dauka cikin gidan. Amma a kowacce rana hasnaa da rumaisa da wasu mata da batasan su waye ba suna ziyartar gidan. Cikin kulawa take ta kowacce fuska,cikin kulawa da tattali take da wani irin gata daya sanya ta soma tambayar kanta,wacce irin rayuwa tayi a baya ne?,gata ne da kulawa ta samu?,ko kuma copy ne kawai na gatan ba original ba?. Abun mamakin yadda kwanyarta ke kwashe komai......ita kanta me dora mata tsarin tana ganin mamaki qarara kwance saman fuskarta. Bawai suna da wani qarfin ikon sauya mata rayuwa bane.....aah ta yarda tabi komai yadda aka tsara saboda tana buqatar fita daga gidan. Tana buqatar sanin WAYE SHI?,tana da buqatar ganin anihin rayuwarsa,hakan kuma dukka ba zata samu ba sai tayi qoqarin maida kanta yadda sukeso. *zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 08187255862 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 08187255862 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽 [5/25, 11:33 AM] +234 916 570 6016: .💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 53 Kuka sosai ta fashe dashi tana qoqarin boye kukanta don kada Aanaani dake zaune tana amsa waya ta jita. Ta lura daidai da kallo ma ba kai tsaye yake kallonta ba. Haka yake kallonsa akan kowacce diya mace yana qoqarin kauda idanunsa a kanki.....amma me yasa sai a yanzun haka yafi zafafarta?. Ta tabbatar ba irin wannan kallon yakewa matarsa ba......bama irin wannan kallon ya mata ba har yaja ra'ayinsa a kanta ba. Me yasa bazai.kalleta da dukkanin idanunsa ba kamar yadda ya kalli matarsa?. Ta tabbatar tana da dukkan wata siffa hali da dabi'a da yakeso game da d'iya mace......ta tabbatar indai zai kalleta yau gobe zuwa jibi.....lallai wataran zata samu kyakkyawan gurbi da muhalli a ransa. Ta sanshi ta karanci dukkan wata dabi'a tasa,tasan abinda yakeso tun daga kan sutura yanayin turare abinci da yanayi(weather)na gari dana muhalli,tayi kuma amfani da dukkan wannan ta fara samar da magana me dan tsaho a tsakaninsu,koda kuwa akan karatu ne amma taci wannan galabar. Ba irin farkon zuwanta ba.....ba kamar a baya ba da daga nesa kurum take hangensa......me zai sanya ta tsaya a iya haka?. "Wacece ita?" Ta samu kanta da tambayar kanta bayan dogon tunanin data gama. A kaf dabi'arsa ta gama gane baya wani ra'ayin mu'amala da mata,baya zurfafa kallo a kansu,wannan ya bata relief na cewa itace kawai zatayi nasarar shiga rayuwarsa. Ta yaya wannan din ta shiga rayuwarsa?,wacece ita?,dame ta fita?,dame take taqama?. Wadannan tambayoyin gaba daya suka kwadaita mata son gani da sanin WACECE AKHNAN. Duk da tana fargaba,zuciyarta kuma tana gaya mata koma wacece zata samu nasarar mallakar sheikh muhammad din tako ina ta cika mace tabbas......to amma kuma tana fata duk cikar da tayi ita ta fita ta kowacce fuska. Tsam nanay ta miqe sanda yake shigowa dakin,fuskarta shimfide da murmushin nan da yake sake nuna dattakonta da tarin nutsuwar da yaranta suka gada daga gareta. Shima nasa idanun suna kanta,yana dubanta da wani kalan tarin qauna da soyayya da tausayi na jiran wasu mutane data dinga yi a rayuwarta na tsahon shekaru ba tare da tana da tabbaci akan komai daya shafesu ba. Ya lumshe idanunsa yana kama hannayenta,yana jin wani irin sassauci da sanyi a ransa a duk sanda ya tuna cewa shine zai zama silar yankewar wannan jiran.....shine zai kusantata da nesanta.....shine zai zame mata tsani na sake rayuwa da mutanen da sukafi soyuwa a ranta. "Zauna nanay" Ya fada yana zaunar da ita saman lallausan tuntum dake zube kan kilishin dake dakin. Bata musa masa ba,ta zauna shima ya dawo gabanta ya zauna saman qafafunsa yana dubanta. "Na dauka kin gaji da jira kin kwanta". Murmushi tayi ta girgiza kai. "Nace zan jiraka muhammad,munyi kewarka sosai.....zanso ace a yanzun haka a irin wannan yanayin surukata tana gefena kamar yadda kake zaune a gabana.....amma al'ada tayi mana wannan shamakin" Ta fada tana murmushi. Yau kawai sai yaji kunyar nanay ta kamashi,yadan sauke kansa qasa. Wai shine da mace?,shine ya auri wata macen?. "Yaya take Muhammad.....gayamin" Da mamaki kadan a fuskarsa ya daga kai yana duban nanay din. Idanunta basu qaryata abinda ya fita yanzu a bakinta ba. Da gaske take tanason ganinta,wacce irin qauna ce wannan?,tun kafin tasan wadda ya kawo mata a matsayin suruka?,tun kafin taga wacece?. Babban abun,a duk lokaci itin wannan da zai dawo daga tafiya ba wanda Nanay takeji ko ta gani saishi,amma a yau maimakon zallar kulawar nan a kansa shi kadai ta soma rabata da wata?. Tun a ranar farko?. "Lafiya alhamdulillah nanay" Kai ta gyada a hankali. "Nace da hasnaaa ta bani ita a dazun muyi magana saita manta.....fatana daya ta kasance me fikira kamar yadda mijinta yake,ta kammala karbar horo cikin qananun kwanaki don ta iso cikin ahali" Qasa yayi da kansa kadan yana murmushi,shi duka ba wannan ba.....izzarta Allah yasa ta barta tayi abinda ya dace,yana fatan izzarta ta barta ta ajiye komai na agadez ta shiga practicing al'adu da dabi'un fada da masarautar aba jifar. "In sha Allah nanay" Ya fada yana zama sosai wannan karon. Hira suka shiga yi a tsakaninsu,irin hirar yaushe gamo. Hirar da take kama da hirar masoyan da sukayi nesa da juna. Abubuwa masu yawa suka tattauna,basa ma ko kallon abincin da tasa aka shirya kala kala daga nau'ikan abinciccikan alfarma na al'adarsu da tasan yafiso. Ya bata labarai kala kala na yadda komai yazo masa. Zuciyarta ta karaya,tayi laushi sosai. Aikinsa a kullum rana tsoro yake sanyata na wanne irin qalubale wataran zai hadu dashi?,amma bata taba yarda ta nuna masa ba. Saboda ta sani,daga ranar daya fahimci abinda yake daga mata hankali,tayi imanin ya ajiye aikin kenan bazai sake waiwayarsa ba duk da yadda yakai ga son aikin. Bata burin ta zama sila ko sanadin hanashi wani jin dadi ko cikar buri na rayuwarsa. Abu daya da take nacewa Allah akai wajen roqa masa shine MACE TA GARI. wadda zata zame masa sanyin idaniya.....wadda zata debe dukkan wani fargaba damuwa da hadari na cikin aikinsa......wadda zata bashi AMINCI ta kuma bashi NUTSUWA. Wadda zata soshi kaman yadda takeson kanta. Wadda zata tare kasa cutarwa.....wadda ba zata bari ya cutu ba tako ina.....uwa uba wadda zata iya dauke dukkan nauyinsa da lalurarsa ta d'a namiji......ta bashi abinda ya kauda kai daga bid'arsa duk da tarin buqatarsa akai.....yayi haquri ya jira halal dinsa. "Nanay" Ya kirata da girmamawa bayan sun kammala cin abincin da ita ta dinga zuba masa har sai daya qoshi. "Sheikh muhammad" Ta fadi da murmushi. Yakanyi murmushi a duk sanda ta kirashi irin hakan,sai yaji sunan kaman yafi dadi a bakinta. "A duniya.....wanne buri ne kike fatan cikarsa kafin ki koma ga mahaliccinki?". Tayi shuru tambayar tana ratsawa cikin kanta. Tana da wasu burika na daban......amma ta sani inde ta riga muhammad rasuwa to zai iya cika mata su,koda bata gani da idanuwanta ba,amma a yanzun burin da take dashi shine taga 'yan uwanta. "Muhammad......burina bana jin me cika ne" Ta fada a raunane. Matsawa gabanta yayi sosai,ya kama hannuwanta ya riqe cikin nasa. "Kija numfashi sosai nanay,ki fadi duk wani burinki,a gaban muhammad dinki kike" Murmushi ya subuce mata dake hade da ruwan hawayen da baikai ga zuba mata ba. "Na sani.....wannan jan gwarzon namijin,zakin d'ana" Maganan ya sashi qaramar dariya,duk da ba yau ya fara jin ta fadi haka a kanshi ba,amma murmushinta kawai ya sanya wani farinciki a zuciyarsa. "Burina naga safiyya da safeena,duk da nasan zai wahala rayuwa ta bamu wannan damar" Ta fadi cikin alamun karaya da yanke tsammani. "Idan na sadaki da koda wani abune daya shafesu......wannan burin naki ya cika?" Samun kanta tayi da qanqame hannunsa sosai har yaji hakan cikin jikinsa,idanunta cikin nasa sosai. "Koda abinda ya shafesu ka hadani dashi muhammad inaji a jikina zai zamana kamar ka hadani dasu ne kai tsaye......amma anya...." "Kisa a ranki a nan kurkusa wannan burin naki zai cika" Har cikin tsakiyar kanta sai da taji wani abu,mamaki ya hanata cewa komai da wata irin shakka data cika zuciyarta. Tafi kowa sani.....ba maqaryaci bane......idan ya fada koda da wasa ne sai ya cika. Wannan ya sanya yake kiyaye harshensa akan fadin abubuwa sosai don baya fadin abinda bazai aikata ba. To amma idan ta gamsu da abinda ya fada fa?. Ta ina zai nemo mutanen da ko burbushinsu ba wanda ya sake gani ko ya sake jin labari shekaru kusan talatin?. Amma kuma gaskiyarsa wata abace da ko yaushe take sake nuna zahirin waye shi. _ki yarda kawai nanay.....mu lu'u lu'u followers muna tayaki murna da haifar jarumi kuma nagartacce,ya rabbi kasa mun haifi sanyin idaniyarmu muma_🙏🏽🙏🏽 ★★★Kwananta daya tak ta soma karbar wasu darussa na sabuwar rayuwar data dinke tunaninta tsaf. Wasu irin al'adu na girmamawa,sutura,yanayin magana da yanayin kula da miji da bata taba ganin irinsu ba. Komai da ake qoqrin azata akai da koya mata mamaki yake bata. Tanason karanta da fahimtar dukka dalilan yin hakan. SARAUTA ta tabbatar gidan wani sarautar ya shigo......gidan sarautar dake da wani irin tsare tsare da tarbiyyar da a tunaninta bata dauka wani gidan sarauta zai kasance irin haka ba. Abu daya da bata gane ba shine......waye shi a masarautar tasu?. A rannan yace mata shi BAWA ne......amma tako ina maganarsa ta gaza shiga zuciyarta da ranta tayi tasiri. Ba wata alama ta bauta a tattare dashi......horon da ake bata kuma baiyi kama da koyarwar da za'a zauna ana yiwa matar bawa ba. Sabuwar rayuwa take shiga......wata irin sabuwar rayuwa da bata taba sanin da zamanta a duniya ba. Sai a sannan ta tuna da zancan aisa. (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) "Duk yadda kike ganin kinsan duniya da yawa,qasashe masu tarin yawa,kin cakuda da mutane qabila kala daban daban......amma akwai inda zaki shiga kiga kin koma kamar wadda batasan komai ba.....rayuwa gaba da gabanta ne.....kafi an fika,Allah ne kawai a sama" Tayi maganan ne tun farko farkon fara zuwan manemanta da sultane ke sahale musu ganinta. Ta raina daya daga cikinsu daya kasance d'an sarkin Cameroon,duk da tarin dukiyarsa da wayewarsa. A lokacin aisa taso ta aureshi......amma ta gaya mata ba'a halicci d'a namijin daya hada dukka qualities din da take buqata daga gurin namiji ba,auren wanda bai hada wadannan nargartar ba tabbas zai zama tozarci ne da qasqanci a tattare da ita,koma baya da rasa martabarta. Wata irin kulawa ake bata.....wata irin girmamawa da tattalin da hatta su birra saida suka raina yadda suke kula da ita a agadez. Komai nata ya canza,daidai da fatarta tasan akwai wani abu daban dake faruwa a rayuwarta. Qamshin jikinta ya zame mata qamshi na biyu dake debe mata kewa bayan qamshinsa.......qamshin turaruka na SHUWA INCENSE AND MORE( +234 704 229 3387) wani qamshi da yake sanyata dadewa cikin duvet duk safiya idan ta farka tana shaqar qamshin yana kai mata har cikin kwanyarta,yana kuma qoqarin kwashe mahaukaciyar kewarsa da takeji tana qoqarin hanata dukkan walwala. Ta dauka a kowacce rana zai shigo ya ganta......ta dauka kowacce rana zata zame masa ta ziyara,saidai abun mamaki babu shi ba dalilinsa. Ba kiransa a cikin kwana biyar din data dauka cikin gidan. Amma a kowacce rana hasnaa da rumaisa da wasu mata da batasan su waye ba suna ziyartar gidan. Cikin kulawa take ta kowacce fuska,cikin kulawa da tattali take da wani irin gata daya sanya ta soma tambayar kanta,wacce irin rayuwa tayi a baya ne?,gata ne da kulawa ta samu?,ko kuma copy ne kawai na gatan ba original ba?. Abun mamakin yadda kwanyarta ke kwashe komai......ita kanta me dora mata tsarin tana ganin mamaki qarara kwance saman fuskarta. Bawai suna da wani qarfin ikon sauya mata rayuwa bane.....aah ta yarda tabi komai yadda aka tsara saboda tana buqatar fita daga gidan. Tana buqatar sanin WAYE SHI?,tana da buqatar ganin anihin rayuwarsa,hakan kuma dukka ba zata samu ba sai tayi qoqarin maida kanta yadda sukeso. *zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 08187255862 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 08187255862 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽 [5/25, 11:33 AM] +234 916 570 6016: .💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 54 Suna waya da shehnaz,aisa da morsa lokaci lokaci......amma har yanzu ta gaza samun sultane sai sau daya tak. Shima maganarsu dashi gajeriya ce......ya mata wata magana a qarshe data sanyata fashewa da kuka. "Gida nakeso na dawo bappi......gida nakeso nazo na ganka" Murmushi ya sake mata. "Nace miki ko bayan na mutu kike kuka ko biftu?" Ya fada da murmushi "To ko mutuwa nayi indai haisam bai lamunce kizo ki ganni ba ban yarda kizo ba.....idan kika bishi hakanne zai samawa ruhina salama koda cikin kabarina......duk da ina lafiya cikin qoshin lafiya,muna kan wani aiki ne da yake janyemin lokaci,duk sanda kika nemeni baki sameni ba....karki saka a ranki wani abu ne mara kyau,cikin aminci nake da kiyayewar Allah". Tayita kiran aisa sa shehnaz ko zataji wani abu,amma ba wata alama data nuna akwai damuwa ko matsala cikin masarautar,haka ahmad data kira shima abinda ta gani kenan,wannan ne ya sanya mata nutsuwa a ranta,ta maida hankali ta kammala wancan training din ta fito,tunda duk binciken da tasa a mata sunce basu gano komai a kansa ba,wannan karon ita zata nuna masa adadin nata ikon. Batasan me yake faruwa ba,tasan dai kawai ta tsinci kanta tsundum da yawan duba wayarta. Duk bayan shudewar wasu mintuna saita duba screen din wayarta,daga haka saita fara zarcewa zuwa gurin kira. Takan jima da wayar a kusa da ita,takan jima tana juya wayar a hannunta,batasan me take jira ba,batasan me take nema ba. Sannu a hankali sai wadannan hotunan data fuskanci da yawa an daukesu ba tare daya sani ba......a mabanbantan lokuta a kuma mabanbantan gurare suka zame mata qawaye.....suka zame mata abubuwan da duk rana ranar ba zata fito ta fadi ba bata buda ta kalla ba. Daga qarshe ta sani.....ta bari zuciyarta tayi mummunan sabo da al'amuransa......sabon da batasan meye dalili ba.....sabon da batasan meye ya kawoshi ba......ta sani ta saba ta saba ta saba......amma duk da haka akwai abu daya dataqi yarda a karan kanta cewa SOYAYYA CE. Yarda da cewa tana sonshi tana jin shine qarya ta qarshe da zata qara yarda zuciyarta ta qulla mata. Ta sani tadade da kashe duk wani gurbi na taso wani d'a namiji a zuciyarta. Ko meye takeji ta yarda ta sallama da cewa SABO NE SILA. Tasha kallon number daya kira a wancan ranar......amma kuma ta dade da yiwa zuciyarta bore wadda ke shawartarta ta gwada kiransa. Yasan inda zai ganta......yasan number da zai kira ya sameta,bai nemeta ba......ta yaya dalilin sabo zata bari alfaharinta na diya mace yayi qasa?. Tana tsoron sabo ya karya wannan alfarmar don haka a wani yammaci ta dannawa number delete,amma batasan me ya sanya wani abu ya tsaye mata a wuya ba bayan ta goge number. Ranar farko da hawaye suka cika mata idanu ranar da kewarsa ta hanata bacci. Tayita juyi,tayi alwala tayi sallah duka wannan kewar data rasa wacce iri ce ta hanata sakat. Me yasa duk yadda na dade da sultane da kowa da kowa dake cikin masarauta bana jin girman kewarsu haka a raina?. Me yasa banquntata da yawa ba daga rashinsu a kusa dani?,saishi?.....WAYE SHI?,meye na musamman a tattare dashi da kewarsa ta dara ta kowa nauyi cikin zuciyarta?. D'isar qwallar kawai taji saman cinyarta,sai wani irin mamaki ya kasheta. "Qwalla akhnan?,qwalla saboda kewar D'A NAMIJI?" Ta jima jikinta a sanyaye tana jin zafin abun. Me yasa ta sake masa haka da yawa?,me yasa ta bari suka saba da ganin juna da jin motsin juna?,wanne irin sakarci tayi haka?. Hannu tasa ta dauke qwallar tana gayawa kanta,har yanzu itace dai akhnan muhammad hammud.....bai kamata ta bari wani abu ya karyata ba,amma dai daga qarshe sautinsa.....qira'arsa.....karatun qur'aninsa ta kunna da qaramin sauti can qasa,shine abinda ya sama mata nutsuwar data samu yin bacci a wannan daren. ★★Duk zirga zirgar daya yini cikinta tsakanin gidan prime minister da gidan governor na jimma a yinin ranar data zama ta qarshe tun daga safiya zuwa yanzun da sararin samaniyar jimma ke bada wata lallausar iskar hadari hakan bai ture tunaninta ko sau daya daga ransa ba. Baisan meye me qarfi da girma haka dake maqale da ita a zuciyarsa ba. Kwanaki ne da suka zame masa cikamakin kwanika masu muhimmanci wajen cika alqawari kan aikinsa. Yayi handling muhammad jinjiri ga ahalin ajani a sirrance bisa sharadin ba zasu bayyana dawowarsa cikin ahalin ba har sai ya kammala nasa aikin......ya rufe file na case din mutuwar ajani,ya miqawa gwamnatin qasar Ethiopia tamim babba tamim qarami da dukka qasurgumayen masu laifin da ake ci dasu cikin haramtaccen gidan villa street da ya salwantar dashi. Abu guda daya ya nema su daga masa qafa suyi masa alfarma shine,gurfanar da zaituna cikin asalin qasarta tushenta,wanda ya buqaci su bashi wasu watanni don komai yazo daidai da yadda ya tsara. A yanzun aikin da ya yiwa qasar ba wata alfarma da tafi qarfin ayi masa ita.......bama wannan lokacin ba.....tun a bayan,yana da wani irin girma kima da martabar da gaba yake da alfarma kowacce iri ce,ballantana a yanzun. Ya sake samun wani girman na musamman,darajarsa ta sake ninkuwa,hakanan ya sake shiga cikin abubuwa masu tsada da darajar da qasar Ethiopia din ta mallaka. Ya dauka ya kammala aikin a kwana biyun kawai,saidai ahalin ajani sun dora masa nauyin daya hada da moti na zuwa kebantaccen gurin da moti dinne kawai ya sanshi inda sauran kaso me girma na dukiyar ajani take. Tafiyar tazo masa da wahala sosai,bai sani ba gajiya jikinsa ya fara yi ko kuwa?. Shi kansa ya sani,a wannan karon yayi aikin daya kamata ya daukarwa kansa da kansa hutu,ya bawa gangar jikinsa dama ta huta sosai. Kwanansu uku a gurin suka kammala komai,aka fidda dukiyar data bawa moti lambar yabo daya iya dauke wannan sirri na tsahon shekarun da amininsa ya buqata. Yawan adadin dukiyar daya gigita kowa,saidai moti ya shaida musu,akwai reshe daya daya rage da ajani ya fadawa wani cikin aminansu. Sun zabi killace muhammad a tare dasu,ya saba dasu zuwa sanda haisam zai bada umarnin sadashi da dangin mahaifan safeena kakanninsa kenan. A wannan yammacin da motocin alfarmar da suke zama tambarin prince sheikh muhammad haisam suke tafiya cikin wata irin nutsuwa saman kwaltar......idanunsa can qasa qasa cike da tarin gajiya......idanun da suke zube saman kwalta yana ganin yadda yanayin ya fara juyewa irin yanayin da yakeso......irin yanayin da tsirrai ke wani irin kyau,yanayin da tsirran ke fidda sabbin ganye masu daukan hankali,su kwantar da duk wata qura da ka iya damun dan adam da walwalarsa. Lafiyayyen agogon fatar da yayi luf saman kyakkyawar fatarsa dake lullube da nu'imtacciyar gargasa ya kalla. Yamma tayi sosai.....amma zuciyarsa yaji tana karkata wani guri na daban a maimakon gida. Wani guri ya dan danna daga seat din gabansa (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) "Mu wuce palace training home" Ya furta da wani nutsuwa da jan aji,jan aji da ginshirar data dadu saboda gajiya da kasalar da yakeji. Daga ta cikin abinda ya danna din aka dawo masa da amsa cikin girmamawa,da alama ya tura saqo ne zuwa ga driver din motar. Maida idanunsa yayi kan kwaltar yana kallonta,kafin a hankali murmushi ya subuce masa,wani tattausan murmushi daya qarawa fuskarsa ajiyayyen kyau. Ya sani.....kuma jikinsa yana bashi,zaije ya tarar da wani yanayi tabbas saman fuskarta. Abinda ita kanta bata sani ba.....abinda ya jima shi kuma da kara tarsa da kuma lura dashi shine. Ita din wata iri macace me son kulawa.....macace meson a damu da ita,wanda hakan qila ya samo asali ne daga fake love da fake caring na mammina. Wadda ta kadaita a dukkan komai,ta tattara kulawarta da damuwarta a kanta a zahiri ba tare data hadata komai da kowa ba. Ta tashi da wannan yanayin,ta saba dashi,shi yasa komai yake zuwa mata a baqo a duk sanda aka dauke kai daga lamarinta. Da gaske yayi busy din da dukka wayoyinsa ma basa hannunsa,ya ajiyesu a killataccen guri. Amma behind hakan akwai wani TARKO da yakeso ya d'ana,akwai wani ANALYSIS da yakeso yayi. Daga ranar da hannuwansa suka kai gangar jikinta,daga ranar da hannuwansa sukakai muhalli da guraben da bai taba zaton zasu je ba.....daga ranar ya tabbatar MUTUWA ce kadai zata iya sanyawa ya zare igiyoyin aurenshi daga kanta,koda mutuwar ma baya tunanin ta isa ta sanyashi yayi hakan. Daga ranar daya qetare iyakar da bai taba qetarewa wata mace ba sai a kanta,....daga ranar daya shiga wani yanayi da babu wata diya mace data taba ganinsa a cikin sa,koda kuwa nanay dinsa......daga wannan ranar ya dasawa kansa MALLAKA......ita din mallakinsa ce.....koda da kallo na idanu zaiyi bakin qoqarin hana kowacce halitta isa gareta ta hanyarsa. Yana da kishi......yana da kishi sosai ya sani,wannan kishin bazai taba bari ya barwa wani ita ba. Koda baiji mafi girman soyayya a ransa ba.....amma ya raba wani sirri nasa da ita,ta ganshi cikin wani yanayi na fitar hayyaci,shi kuma bazai taba bawa wani d'a namiji hannuwansa sukai kan inda nashi hannun suka kai ba. Idanunsa ya lumshe yana jin tunaninsa kawai na qarshe kaman an dora masa wuta saman zuciyarsa,sai kawai ya miqa hannu yana sassauta necktie din dake daure a wuyansa cikin lafiyayyar luxury suit din jikinsa da kalarta ta fidda anihin ma'anar kalmar KYAU a tattare dashi,ya maida idanunsa ga hanya sanda suka fada titin da zai sadasu kai tsaye da qofar killataccen gidan. ~Da wannan miskilar fuskartata take zaune birra na qarasa daure mata dogon gashinta a tsakiyar kanta. Fuskarta tayi wani fayau,wani irin ajiyayyen kyau na samun ninkin kulawa da wani sirrantattun abubuwa da batasan amfaninsu ba da suka ratsata. Da farko batasha saboda bai mata kama da abun al'adarta ba,amma daga qarshe zenabu ta zauna ta amintar da ita tasha cikin hikima. Kuma koda tasha din ya mata dadi a baki,ya mata kama da wani abunsha da sukanyi na al'adar buzaye,tun daga ranar bata sake musun sha ba. A girmame aka nemi izinin shigowa sannan aka turo qofar,bata damu ta waiwaya ba,ta zubawa kanta idanu ta ciki madubi tana kallon yadda shigar kayan sukuwar dokin suka mata kyau. Qoqarin kokawa takeyi da tunaninta da dukkanin iyakacin qarfinta......qoqarin koyawa kanta rayuwa takeyi dashi ko ya nemeta ko bai nemeta ba,shi yasa yau da yammar nan ta buqaci a shirya mata doki zata hau cikin gidan tayi sukuwa a faffadan filin wasannin ball dake cikin gidan. Alitash ce,daya daga cikin hadimanta na cikin gidan,wanda sosai takejin dadin zama dasu kamar yadda suke dasu birra. Wasu irin bayi ne data rasa wanne irin horo aka musu haka na iya faranta ran ubangidansu da duk abinda yakeso a sanda ya dace?. Ko a yau da tace tanason hawan dokin,ta dauka a yadda tsare tsarensu yake zasu hana,amma sai gashi tana cikin bathroom tana wanka suka shaida mata an gama shirya komai. Zenabu ce kawai taso tadan mata gyara kan shigar da tayi. Wando ne skinny daya kama jikinta sosai,ya fidda kowanne lungu da saqo da tudu na jikinta,kamar yadda fingilalliyar rigar itama ta fidda dukiyar fulaninta kamar ka saka hannu ka cirosu,suka kuma fidda plate tummy dinta kamar bata taba sanya masa abinci ba tunda Allah ya halicceshi,saidai kuma daga baya ta sanya aka yiwa gurin tsarin da daga ita sai hadiman data zaba su shiga harta gama hawan nata,basu kuma sake cewa komai ba. *zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 08187255862 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 08187255862 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 55 "Allah ya qara daukaka darajarki.....an kammala" Ta fada da girmamawa. Tadan juya ta kalli alitash,sai kawai suka burgeta. "Na gode......" "Amhara tace ko zaki fara cin wani abu?" Alitash ta fada da kulawa. Kai ta gyada a hankali,ba shakka zata iya bawa hadimai da bayin agadez maki casa'in ta cikashewa wadannan zuwa dari bisa dari. Ta fahimci zataje din,saita miqe suna mara mata baya zuwa parlor din da tafi zama cin abinci. Falon yana cikin falukanta da tafiso a 'yan kwanakinta cikin gidan. Komai ya kasance da tsarin gargajiyar dake nuna al'adar oromia. Wasu abubuwan nasu suna burgeta,amma yadda ba wanda yace mata komai,ba wanda ya taba mata bayani,itama bata damu ta daga kanta ta tambaya ba. Kafin ta qaraso sun saita mata takalman da zata sanya ta cire wadanda ta fito dasu a qafarta kamar yadda suka saba,ta zare wadancan ta saka wadanda suka batan,ta fara takawa a nutse tana nufar traditional royal dining table din. Ta san abinda tafi buqata a yammacin,abinci mara nauyi,koda ta makara bataci abincin rana ba,don haka bata takurata da tambayarta me zataci ba,ta soma serving dinta. Wani lafiyayyen farfesu ne me romo sosai data lura akhnan din tana matuqar so cikin irin abinciccikansu. Yana tattare da wani sirri sosai a cikinsa,ta zuba mata oromian black tea daya kasance royal black tea ne saboda tsadar ganyayyakin da ake dafashi dasu,ba gidan kowa kake samunsa ba,kamar yadda ba kasafai ake samunsa ba duk da sune suke nomashi,ta saka mata spoon da fork,sannan dukkaninsu suka tattara suka bar mata parlor din saboda sun karanci bata fiyason cin abinci cikin mutane ba. Tun daga gate din farko da motocinsu suka tsaya aka soma bude dukkanin qofofin gidan da wani iri salo na karramawa da girma. Motocinsa daban suke.....cikin fadin Ethiopia dama qasashen dake maqwabtaka dasu,cikin qanqanin lokaci hadiman dake gidan gaba daya suka zagayeshi cikin marabta ta girma,ya kuma gaisa da kowa cikin mutuntawa da sanin daraja da kimar da Allah ya yiwa dan adam,kafin kowa ya qyaleshi,ya juya ya soma takawa zuwa cikin gidan a nutse. Duk wani setting room ko parlor da zai wuce cikin matuqar girmakawa hadiman dake gurin suke zubewa su gaidashi,sannan kuna su zare jikinsu su fita don sun tabbatar yau yazo ganin gimbiya ne. Baya da dabi'ar son a zube a gaidashi,amma duk yadda yayi dasu sun gaza dainawa. Sunajin ba zasu iya daina gaidashi ta hakan ba,girma da kimarsa da mutuntakar dake tsakaninsu tafi qarfin su iya gaidashi daga tsaye. Kai tsaye ya zarce zuwa parlor din,ya tabbatar tana can,don yana da analysis na motsinta cikin gidan,yana da rahoto kan duk wani abu da tafiso. Wata irin qofa ce da bata bada alama ko sauti ko daya yayin budeta,wannan ya sanya hankali kwance ya janye qofar gefe,ya kuma saka qafarsa a parlor din idanunsa suna dauko masa hotonta a matsayin abu na farko da suka fara gani cikin falon din. Tana zaune saman kujerun,ta dafe gwiwar hannunta dukka biyun da table din. A hankali take juya tea din idanunta cikin cup din,kallo daya zaka mata kasan akwai wani d'an qaramin tunani dake mata kai kawo cikin ranta. Yadda tadan karkatar da kanta ya sanya jelar sumarta da aka fake a tsakiyar kanta ya dawo kafadar hagunta yake reto a hankali daga bayanta zuwa gefan fuskarta. Ta gama juyawa,ta ajiye spoon din a gefe,ta daga mug din ta soma kurba a hankali. Labbanta yabi da kallo,labbanta da hucin ruwan dumin ya sake sanyawa suka sake canza kala.....a idanunsa sunyi looking very soft,abinda ya soma tayar masa da tsumin data dasa masa a dukka gangar jikinsa tun a wancan ranar. Idanunsa ya zame a hankali zuwa santala santalan qafafunta,yayi sama da dubansa har zuwa qugunta daya fito sosai ya bayyana bajajjun mazaunanta da suka dace da shafaffen cikinta. Yadda ta zauna saman kujerar ba'a daidai ba ya sake fidda shape dinta sosai,ya kuma sake fidda fadi da tudun mazaunanta,don ta karkace bangaren damanta ne sosai,sai hakan ya zamana kakar da gayya ta turosu daga daya side din. A hankali yaci gaba da bin sassan jikin nata da kallo,har zuwa sanda ya kawo kan mutanen nasa. Wannan gurin da kallo daya tak ya masa yaji kaman qafafunsa ba zasu iya daukarsa ba......sai kawai ya zube hannuwansa cikin aljihun trouser dinsa ya jingina kafadarsa da jikin qofar,yayi crossing qafafunsa kawai yana ci gaba da narke idanunsa a kansu kamar an bashi aikin kallonta,ko kuma wanda ya shiga gasar iya kallo ta duniya. "Ya salam.....ya salam sallim sallim" Ya furta yana jin yadda ake jona masa wani wiring na shocking cikin jikinsa gaba daya. A cikin jikinta ta soma jin she's not comfortable ba kaman dazu ba,amma sanin cewa ita kadai ce cikin gidan ya sanyata jawo plate din farfesun,ta sanya spoon din,amma ta gaza kaiwa bakinta sai juyawa take a hankali. Ta kusa minti daya kafin takai na farko bakinta,yabi dan qaramin bakinnnata da kallo,yana tuna yanayin daya shiga wancan lokacin daya hade bakunansu guri daya......yana tuna abinda ya dinga ji da yadda kowacce wuta ta jikinsa ta dauke masa. Tana zare spoon din daga bakinta idanunta suna sauka a kansa. Wani bugawa zuciyarta tayi da kyau,bugawar data haddasa mata qwarewa ta ajiye spoon din ta fara tari. Da sauri ya zare hannunsa daga aljihun wandon ya fara takowa sa sassarfa. Kai tsaye ya isa gaban table din,ya dauki gorar ruwan data kasance ruwan kamfanin masarautar ne,ya bude ya tsiyaya mata a cup a gaggauce ya miqa mata. Ta miqa hannunta tana yin tarin a hankali,ga zatonta zai sakar mata cup dinne,amma sai taji ya hada harda hannunta ya riqe gam ya isar da cup din bakinta,sai data fara sha sannan ya zare hannunsa a hankali ya koma da baya a nutse ya zauna saman kujerar dake opposite din tata yana kallonta. Komai nata da jan aji,komai nata akwai isa a ciki,ko yadda takeshan ruwan kawai zakasan akwai ginshira cikin lamarinta. Cire cup din tayi daga bakinta,sannan ta soma ajiyeshi a nutse tana sauke numfashi. Idanunta ta daga ta aza a kansa. Still kallonta yake kaman Allah ya aikoshi,fuskarta ta hade sosai tana jin bugun zuciyarta har yanzu bai daidaita ba. Batason wannan kallon......yana sanyata ta daburce gaba daya.....batason wannan kallon saboda yana karanta mata kai tsaye abinda yake cikin zuciyarta. Bataso ta nuna masa rauninta ko wani abu makamancin haka,don haka ba zata tashi ta bar masa gurin ba,hakanan batasan me zatace dashi ba tunda sai yau ya tuna da ita?,don haka ta sake jawo plate din ta maida spoon din da zummar ci gaba daci,amma kallonsa a kanta yayi yawan data kasa hakan,sai kawai ta zabi ci gaba da juya spoon din. Ya fahimceta duk da batace komai ba,baijin zai iya hana kansa ci gaba da kallonta.....bayajin kuma zai cuci kansa ya janye idanunsa daga kanta,halal ce.....halal dinsa ce.....wannan kallon da yake mata na halal ne......wannan kallon da Allah zai bashi lada ne.....wannan kallon da Allah zai saka ya sake yarda dashi ne,don bai kalli d'iyar kowa ba......bai kalli halalin kowa ba sai nashi. Spoon daya ya zaro shima cikin wani hadadden abu na silver dake gefe wanda aka adana spoons din a cikinsa. Kai tsaye ya zura cikin bata kwanon,ya kuma yi bismillah ya debo ya fara kaiwa cikinsa. Yunwa yakeji.....yunwar da bata tashi ba sai a yanzu da yaga abincin gabanta. Yana lissafe kwanaki daya daya har kwana biyar bai zauna yaci abincin kirki ba,uwa uba kuma ga mura da yakejin alamu tana son kamashi. Duk wannan tunanin duk wannan zaman duk wannan cin naman da yake bai dauke idonsa a kanta ko na second daya ba. Tako ta ina......ta kowanne bangare ya takurata. Kallonsa wani irin dafi yake sauke mata a jikinta wanda ba zata iya jura ba,duk iya yadda take zaton tana da zarrar da zata iya basar masa saita dinga jin kamar idanunsa suna yaye mata kowacce sutura dake jikinta,suturar da wata irin nadamar sakata tazo ta mamayeta,don daidai da bugawar da zuciyarta takeyi ta tabbatar yana iya gani ta d'amammen qirjinta. Batayi qarya ba.....idanunsa suna kai.....idanunsa suna ankare da wajen yana irga adadin bugun zuciyarta daya tabbatar adadin ya zarta yadda ya kamata ya kasance. Can qasan ransa ya saki murmushin da bai nuna a saman fuskarsa ba. Ya sani fushi take,fushin da ya tabbatar koda ya gaya mata dalilin yinsa ba yarda zatayi ba. Idanunta ta maida kan plate din da tun naman farko bata sake kai komai bakinta ba,amma yana dab da cinye naman gaba daya. "To zaman me nake?" Ta tambayi kanta,sai kawai ta ture kujerarta baya da zummar miqewa,saidai kuma kawai taji tattausan tafin hannunsa saman bayan hannunta. Wani irin abu ya tsarga mata yarrrr a jikinta,tana jin wata kewa me nauyi na wannan tattausan tafin hannun tana ratsata,amma a zahiri saita hade rai ta daga blue eyes dinta ta watsa masa. "Zaifi kyau ki zauna mu sasanta a nan your royal highness" Ya fada softly yana sake kasheta da wadannan abubuwan dake cikin narkakkun idanunta. (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) Idanma saqo ya aike mata da gaske ya isa har tsakiyar zuciyarta,taji kaman an ragewa qafafunta qwari,to amma ba zata taba yarda ba. "Me ya faru?,me zamu sasanta?,ba abinda kayimin,kawai zamanka a nan ne banaso,ka tafi" Sune kalaman da takeson gaya masa,amma kamar daukewar ruwa suka dauke daga bakinta,sukaqi bata hadin kai ballantana ta furtasu. Abu daya tayi shine zame hannunta,ta kuma juya ta soma sauka daga gurin,abinda ya bashi full access na ganin komai da komai,da yadda suke juyawa da wani irin yanayi daya fusgi hankalinsa,ya kuma sanya naman tsaiwa saman bakinsa,kafin ya tattara qarfinsa ya hadiyeshi da qyar. Sai kawai ya daina jin duk wani taste na naman,wannan dadin da ya masa ya dauke daga kan harshensa gaba daya,sai ya miqe a nutse yana ture tasa kujerar baya,ya soma takawa da kuzari da burin cinmata sanda take shiga parlour din da daga shi sai bedroom dinta. Tsaiwa tayi tana zare takalman qafarta don musanyasu da bedroom slippers,ta saka qafa daya,tana zura qafa dayar kawai taji an mata wata kyakkyawar runguma daga baya,rungumar data tabbatar duk iya qarfin halinta bata isa ta qwace ba,rungumar data sanyata taji tana narkewa cikin jikinsa gaba daya,shu'umin turarensa yana gaya mata MUHAMMAD HAISAM NE. *NA BIYAKU BASHINKU NA JIYA DAI KO?* *_Assalamu alaikum warahmatullah_* *_Na gode sosai,na gode da jumurinku,duk da na dauka zamu fahimci juna ni daku sama da haka,shi yasa na yita dagewa ina baku pages sama da yadda nake bayarwa,ashe da saura_* *_Ko nawa kake samu a komai ma.....dan adam ne kai akwai gajiya,kana buqatar hutu,ballantana rubutu da yake cinye awanni mafi rinjaye na rayuwarka_* *_kin taba biki na tabbatar,kinsan yadda hidimarsa take,yaushe kika samu kanki sanda kuka fara naki bikin?,yaushe kika gama nutsuwa duka kika koma daidai?_* *_wannan rubutun da kuke ganin muna muku shi,wallahil azeem ko baci ranki yayi a rana bakya iya rubutun,koda kin takura kanki kinyi kowa pages din zasu zowa me karantawa ba armashi,koda yara ne suke gida baka samun nutsuwar yinsa,har sai basa kusa dake,walwala kike buqata,nutsuwa kike buqata ta gaske kafin yin kowanne page_* *_wannan ya sanya sau tari da zaku gane haka don marubuci yayi ALLAH YA ISA ga wanda ke fidda masa pages ba zaku zargeshi ba_* *_shi kadai yasan takura da quncin da yake fuskanta kafin ya hada kowanne page,a haka me sata ya fitar yake zaton ZAICI BULUS A GABAN ALLAH?_* *_Ina amfani da wannan damar na shaida ma masu fidda mana pages ta kowacce hanya cewa,zanta gayawa Allah inde ban taba satar miki komai ba....ban taba cutar miki da komai ba......to Allah ubangijin al'arshi yayi min sakayya Allah ya isana duk wadda ta fitarmin da pages ta kowacce fuska kuwa,Allah ya sakamin_* *_Yadda muka killace haqqinmu kayanmu,kuka watsawa duniya UBANGIJI KA BANKADE SIRRINTA DA TAKE ALKINTAWA A IDANUN DUNIYA,ALLAH KARKA SUTURTATA HAR ABADA_* *_Na gode da jumurin bina da kuke,kuma in sha Allah next time labarinmu zai zamana pages saba'in tamanin kamar yadda aka saba book a baya ayi a qarqareshi_* *zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 08187255862 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 08187255862 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 56* Ta bayanta daya rungumetan ta dinga jin wani abu yana ratsowa yana watsuwa zuwa ga sassan jikinta. Ko ina na jikinta ya dauki rawa saboda wannan rungumar ta daban ce.....wannan rungumar tasha banban da wadanda ya taba yi mata. Ya matseta sosai cikin jikinsa yana sauke mata numfashinsa cikin kunne. Dukkanin wata tsiga ta jikinta ta zuba,har batasan sanda ta riqe hannayensa dake riqe da qugunta ba tana jin zuciyarta kamar zata b'allo qirjinta ta fito. Da wani irin zafin nama ya juyo da ita gaba dayansa yana hana kowacce tazara shiga tsakaninsu. Sukayi musayar numfashi lokaci guda kaman yadda qwayar idanuwansu ta hade guri guda. Qirjinta ne kawai ke dagawa sama da qasa saboda wani irin tsoro daya shigeta,dukkanin idanunta cikin nasa tana duban qwayar idanuwan nan nasa da suka birkice gaba daya. Sosai take jin saukar numfashinsa akan saman fuskarta,da wani irin yanayi cikin qwayar idanunsa me zafi,yana yin daya sanya ta zabi rufe idanuwanta ruf tana sake jin yadda yake bada kusanci a tsakaninsu. Ta rufe idanunta ne kawai don bata da qarfin jure abinda takeji,GARWASHI kawai take hanga cikin idanunsa,wani irin abu me kaifin gaske dake sukar zuciyarta da wani irin abu me tsananin kaifi,yana ajiye mata wasu ciwuka da batasan ranar warkewarsu ba. Cikin kunnuwanta takejin cakuduwar numfashinsu guri daya da wani irin banbanci da yabar mata mamaki a tsakiyar rudanin da take ciki. Nasa numfashin me wani irin nauyi ne,ba kamar nata da yake fita da sauri ba. Wani irin riqo ya sakeyi mata yana jawo qugunta ya manne da jikinsa. Numfashinta ya kusa qwacewa da wata irin shidewa da sai daya tallafota da kyau,yayi mata kyakkyawan riqon dake nuna bazai barta ba. Hannunsa daya ya sanya ya daga habarta yana kallon qwayoyin idanunta da suke a rufe,saidai duk da haka ga tudunsu nan don Allah ya hore mata baiwar qwayar idanu. "Regarde-moi dans les yeux(kalli cikin idanuna)" Yayi magana da harshen faransanci,muryarsa can qasa,kamar wanda yake gudun wani yaji abinda yake fada "Ya salammm" Ta fada can qasan maqoshinta tana jin ta fara rikicewa. Ashe duk sanda zai magana da ita da faransanci a nesa take dashi?,shi yasa batajin yadda kowanne harafi yake fita da wani irin nauyi daga bakinsa......da wani irin qwarewa da wani irin accent da salo na sarrafa harshe?. Me yasa a daidai kunnenta haka zata faru?. "Ki bude idanunki" Ya sake fadi yana sassauta riqon da yayi mata,saidai yana qaa tsananta kusancin da yake tsakaninsu da wani irin yanayi da yasa ta soma narke masa a jiki,qafafunta suka fara barazana qin daukarta. Kaman ya gane hakan,sai ya sake riqeta sosai cikin jikinsa yana mata kyakkyawan masauki. "Ki kalleni biftuuu" Ya fada da wani irin taushi da sanyin daya karya mata zuciya,ya kuma sanya hawaye taruwa cikin idanunta. Wai baya gani ne?,baya lura da yadda zuciyarta ta fara narkewa?. Tayi qanqanta da yawa......tayi qanqanta da daukan yadda yake mata magana haka. Bata saba ba.....ba'a taba mata magana da irin wannan yanayin ba..baya ga haka ma kuma sai ya shigo mata kanshi tsaye?. Baiga laifin da yayi ba yakeson lallai sai ya sanya ikonsa da qarfin qwanjinsa ya zagwanyar mata da zuciya?. Besan zuciyarta batayi wannan girman ba?,batayi wannan qwarin ba?. "Bude idonki" Ya sake fada yana aza habarsa dake cike da tattausan sajen dake fidda wani kalan qamshi na daban yayi maganan da low tone sama dana dazu. Ta fahimci da gaske saita bude idanun,ta fahimci rashin bude idanun nata daidai yake da ci gaba da sauke mata ruwan rokoki a jiki da zuciyarta daga sautinsa qamshinsa da yadda ya tilasta cakuduwar jikinsu guri daya. Da ruwan hawaye a idanunta ta bude blue eyes dinta da launin ya cakuda,sai ya riqe fuskartata da kyau cikin hannuwansa yana dubanta da wani irin kusanci. "Bance karki tafi ba?,bance ki jirani ba muyi magana ba?" Ya fada a narke kaman wanda ke shirin sakin kuka. Abubuwa da yawa......abubuwa masu nauyi yake gani cikin idanunta,fiye ma da yadda ya zata. Wasu irin alamu da suka sanya ya fara tantamar anya a yau karatun kai tsaye daga zuciya zuwa cikin idanu basuyi masa kuskure ba?. "Why?....me yasa?" Ya sake fada idanunsa suna qanqancewa,dukkan jikinsa yana saki. Girgiza masa kai kawai takeyi ta kasa cewa komai,duk da yadda taso ta dakatar da hawayen fuskarta abun yaci tura,sai kawai suka gangaro ta gefe da gefan idanunta. Da kallo yabi hawayen har suka dige.....wani hawaye da suke qyalli a idanunsa kamar sunfi na kowa kyau da haske. "Kuka?" Ya tambayeta da wata murya da tafi kama da muryar wanda yasha giya ya qoshi. "No" Ya fada yana girgiza mata kai,sai ya sake riqe fuskarta sosai cikin hannunsa,ya sanya fuskarsa cikin nata,sai kawai ta tsinci harshensa saman fuskarta. Lashe duk wata hanya da hawayen yabi yakeyi yana sauke mata wani irin rikitaccen numfashi. Cikin lokaci madan ta dimauce ta rikice,qoqarin magana take.....qoqarin roqarsa take amma kaman yasan hakan zatayi saiya hade bakunansu guri daya da wani irin zazzafan kiss. Wani irin kiss da yasha banban matuqa dana wancan ranar,tana jin sanda qafafunta suka saki gaba daya suka gagara daukarta saboda ba wani kuzari da karsashi daya rage musu. Tana jin sanda ya sanya ragowar qarfin daya rage masa ya tallafesu gaba daya shi da ita ya qara taku uku zuwa hudu shi da ita dake cikin jikinsa ya qarasa dakin dasu. Shi bai iya wani dogon tsaiwa ba suka zube gaba dayansu saman gadon da baida nisa da bakin qofar. Wani kyakkyawan riqo yayi mata kamar wancan ranar,ya hana bakinta aiwatar da komai,sannan taji hannunsa yana laluben zip din da shine ya hade gaban rigar tun daga sama har qasa. Tsoro ne ya kamata,wani irin tsoro daya sanya cikin rawar hannu ta cafki hannunsa ta niyyar janyewa,shi kuma kawai sai ya sakar mata nauyinsa gaba daya. Nauyin daya sanya qirjinta qara nauyi,numfashinta ya dinfa fita da wani irin yanayi. Hannunsa ya cusa ta tsakanin qirjinsu ya lalubi zip din,ya masa kyakkyawar zuga guda daya tak sai gashi yakai qarshe. Qaramin hauka ya shiga sanda idanunsa suka kai masa kan albarkatunsa. A yau ma ya taki sa'a,ba bra saboda rigar me roba ce,ta hade mata jikinta sosai. A wancan ranar ba wadataccen haske......a yau kuwa haske ne tarwai da zai baka daman ganin koda allurarka ce ta fadi. Wani guri wani muhalli da yake ganinsa a yau a bayyane lullube da farar fatar data sake qawatasu. Tunda hannayensa suka isa gurin komai ya tsaya cak da aiki cikin qwaqwalwarsa,ya daina gane komai sai wani irin saqonni da yake aike mata masu zafi da gusar da hankali. Karon farko ta fara qoqarin bore.....karan farko ta fara qoqarin tawaye,saidai cikin minti goma ya soma kaita wata duniya ta daban,duniyar da batasan da ita ba. Wani hargitsatsen yanayi suka shiga shi da ita,sosai jikinta ke karbar saqonninn da suka sanya bugun zuciyarta zarta kima sama da kowanne lokaci da zata buga din. Zuciyarta ce hautsine da wani irin tsoro sanda yake qoqarin rabata da skinny jeans din jikinta.....wani abu guda daya da yaji ya zame masa wani qatoton waigi.....ya zame masa wata babbar barazana me wahalar fuskanta......kamar dai yana shirin ture dutsen dala ko gauron dutse daga ainihin mazauninsa. Ta samu bakinta a yanzu,don haka gam gam ta riqe hannunsa,saidai ba riqe hannunta ne kawai ba,don bata da wannan qarfin,sunan bappi data sake kira masa ya zare duk wata laka ta jikinsa. Bai matsa daga jikinta ba.....saidai ya sauke mata nauyinsa ta side daya kawai,kwanciyar rub da ciki yana daga sama,ya qanqameta sosai cikin jikinsa yana jin kukan da take rerawa. (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) Bai shirya sakinta yanzu ba.....bai kuma saketan ba,har sai da dumin jikinta da laushin fatarta ya samar masa nutsuwar da yake qoqarin samu. Kaman an fusgeshi haka yayi,ya sake qanqameta kaman zai ballata,abinda ya sake bata tsoro kenan ta kuma fashewa da kuka. Wannan karon me sauti ne kukan,wannan lokacin ba iya hawaye kawai bane. Tsoro yake bata sosai da gaske a duk sanda ya shiga irin wannan yanayin,sai ta dinga ganinsa kamar ba shine ba.....kamar ba shine ainihin sheikh din data sani ba. Gumin da yake fita a goshinsa zuwa jikinsa ya soma nasarta,ta cikin t-shirt din suit din jikinsa data rage gumin yake ratsowa da gaurayen qamshin turarensa yana nashe mata jikin fatarta. "Wanne irin ci amana ne wannan?,saina gayawa bappi,tunda ai yace amanata ya baka" Ta fada muryarta tana rawa sosai kukanta yana sake qaruwa. Da farko maganan ya masa bambarakwai,sai ya saki wani kasalallen murmushi yana cusa fuskarsa cikin wuyanta yana zuqo qamshinta da kyau,amma yadda ta saki kukan da gaske ya sanya yace bari ya gwada. Qasa ya koma ya birkitota samansa yana qarewa fuskarta kallo wadda doguwar sumarta da aka gyara a dazun ta hargitse ta musu rumfa shi da ita. Tun a dazun tun farkon shigowarsu dakin ya zare siririn band din da aka daure gashin dashi,ya kuma cusa fuskarsa sosai cikin gashin yana shaqar daddadan qamshin hair mist na kamfanin SHUWA INCENSES AND MORE dake tashi da wani sassanyan qamshi me halaka nutsuwar zuciya(+234 704 229 3387). Hannu ya sanya yana maida gashin zuwa gadon bayanta,ya taso da wani irin zafi zai soma sauke mata sabbin saqonnin daya tabbatar a wannan karon ba zata iya tabuka komai ba.....saidai tun kafin hakan ya faru manyan idanunta suka firfito waje,ta saki kuma sosai tana tokare tafin hannunta saman lallausar gargasar qirjinsa don tuni button na rigarshi ya zame yayi nasa guri. "Kayi haquri" Ta fada cikin sigar ban tausayi. Maganan yazo masa a bazata.....wani irin ba zata da bai taba zato daga gurin ta ba. Ta cikin idanunta yaga tsoro qarara,tsoron daya sanya kokwanto da mamaki me dimbin yawa a ransa. Sai ya zameta gefe,amma duk da haka bai saketa ba saboda rawar da jikinsa yakeyi bai gama daidaita ba,sai ya bude qirjinsa sosai ya sakata a ciki yana sauke numfashi. Sautin kukanta ke tashi kadan kadan,sakinta kawai takeso yayi ta matsa gefe. Wani irin rayuwa take gani daban da bata taba kawota a kanta ba. "Kiyi shuru......" Ya fada a hankali,saidai hakan bai mata tasiri ba sam. Ya lumshe idonsa muryarsa can qasa ya sake fadin. "Don Allah" Kalmar ta fito mata da wani sanyi daya sanya a hankali sautinta yayi qasa. Bawai ya samu dukkanin nutsuwa bane.....amma yana qoqarin kame kansa ne kawai. Mamaki ne can qasan ransa. A shekarunta?,a wayewarta?,tana nufin bata da masaniya akan irin wannan abun?. Kamar bazai gamsu da haka ba.....amma wani halint guda daya tal na fadi da yin abu kai tsaye ya sauya akalar tunaninsa. Ya tuna yadda ta sauyawa falaak bayan ta tabbatar da abinda ya faru,t juya kaman haushinta takeji......wannan duka yana cikin tarko da plan din mammina?,ko tsabar yadda ta killacw rayuwarta take sarrafata cikin tafukan hannayenta ya kawo mata wannan naqasun?. Baida amsa sam,don haka ya mirgina da sauran kuzarinsa don sauka yayi wanka,don a lokacin yanayin duhun magariba ya tabbatar masa an riga an kammala sallar magariba din. Miqewar da yayi yaji mararsa a qulle sosai. Zafin ya ratashi sosai,yasan hakan zata iya faruwa,don lokaci lokaci yana fuskantar irin wannan issue din. *zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 08187255862 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 08187255862 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 57* Duk da haka ya taka a nutse yana wucewa bathroom. Ta mirgina tana sake qudundunewa cikin duvet. Da gaske kuka take,tana jin ranta yana baci,ba wani d'a namaji daya taba ganin koda singalilin hannunta,amma shikam yanzu ba inda hannunsa baikai a jikinta ba sai gu d'aya tak. "Dama shima haka yake?" Ta fada can qasan ranta tana tuna falaak. Falaak din da har yanzu take mamakinta,don zuwa yanzun ma ba'asan a wacce qasar suka yada zango ba,don ba'a maganan zuwansu Ethiopia yanzu. Motsin fitowarsa ya dawo mata da tunaninta,ta daga idanunta a sace ta qasan duvet tana satar kallonsa,saidai ba shiri ta zuqe kanta ta.maidashi cikin duvet din jikinta na rawa. Towel kawai ya dauro,towel din da ya fara ne kawai daga qugunsa ya rufe iya shafaffen cikinsa. Dukka muscles din da suka lullube jikinsa a bayyane suke,wani siffan qarfi sosai da dama koda ta cikin jallabiyyarsa kana iya ganin alamun hakan. "Zaki iya tashi?,ko kina buqatar taimako?" Ya fadi sanda ya kammala maida kayansa neat,saidai kuma bai saka 'yar saman suit dinsa ba,hakan ya sanya kana iya ganin dan squeezing din rigar tasa tayi. Yayi maganan ne yana tsaye daga can gefe,ya saba 'yar saman suit din nasa a kafada. Zabura tayi da maganan da yayi,tana tuna wancan ranar da yaso daukarta cak ya kaita bathroom din,saita tattare duvet din yana rinjayarta tayi bathroom din. Murmushi kawai yayi,wani kalan murmushi dake qunshe da manufofi da dama. Akwai wasu abubuwa masu yawa tattare da ita......wasu suna bashi mamaki ne suna kuma sauya akalar tunaninsa a kanta,wasu kuma sanyashi suke yana tantamar anya itace?. Ta jima sosai a bandakin,ita daya tana kumbure kumbure gami da share hawaye. Itakam inda tasan haka yake da bata yarda ta biyoshi ba,koda meye sultane zaiyi kuwa. Yanzu da wanne ido zata kalli sultane?,me zatace dashi?. Ba sultane kadai ba,kowa ma gani take zai iya ganin komai a jikinta. Amma abun haushin,abun takaicin,maimakon taji tsanarsa a ranta ko haushinsa.....saita laluba zuciyarta taji babu ko daya,sai alamun saukar hannuwansa a jikinta da takeji tako ina,kamar a yanzu komai yake faruwa. Ta fito daga wankan bayan dadewar da tayi,tanaso ya tafi ne don batasan da wanne ido zata kalleshi ba. A yau dai kam bata da wannan juriyar.....bata da wannan zarrar da zata iya hada idanu sam dashi. Knocking da akayi na qofar ya saka gabanta faduwa,ba'a shigo ba,saidai taji sautin muryarsa daga waje. "Idan kin gama shiryawa ki fito,lokacin sallah zai wuce". Baki ta tura gaba,me yasa bazai tafi ba?,wai me yasa ma bayajin kunyarta ne?,sai ya gama lalubeta hankali kwance kuma yaci gaba da harkar gabansa hankalinsa kwance?. Da qyar ta kammala shiryawa cikin wata yalwatacciyar abaya royal blue data haska fatarta sosai. Kamar me tsoron haduwa da wani abu take kowa inda yake. Yana zaune very calm,kamar ba shine ya danneta dazu dazun a daki ba ya gama lalube komai nata ba. Coffee yake sha cikin wani mug,idanunsa suna kan wayarsa daya ajiye a table din gefansa,batasan abinda yake kalla ba. Narkakkun idanun nan nasa ya dago ya zuba mata,ta janye dubanta da sauri. Me yasa a duk sanda ya gama mata wannan abun maimakon taji ta tsaneshi.....ko tana jin haushinsa.....ko girmansa da kimarsa sun zube saidai taga ya sake mata wani kwarjini na musamman?. "Bismillah" Ya fada yana hawa saman lallausar abar sallar dake shimfide tana fuskantar alqibla. Wata irin nutsuwa,wani irin kwanciyar hankali taji yana ratsata sanda yake rera karatun alqur'ani a duka sallolin. Har taga kaman ma yayi saurin idar da sallolin gaba daya,duk da bayan sun idar ta duba agogo sai taga mintunan daya dauka sun ninka adadin mintunan data saba yi idan zatayi sallarta ita kadai. Wani irin shuru ya ratsa gurin,tayi qasa kawai da kanta,tanason miqewa ta wuce ciki amma zuciyarta ta gaza bata wannan qwarin gwiwar,kawai sai ganinsa tayi ta juyo yana fuskantarta,ya kuma zauna sosai saman dardumar. Dukkan idanunsa ya zuba mata,a hankali kyawawan labbansa suna motsawa yana karanta azkar din bayan sallame sallah. Kafin ya kammala azkar din ya sanya zuciyarta tana dab da rikicewa,ya shafa addu'ar sannan yaci gaba da kallonta kamar abinda yazoyi duniya kenan. "Me yasa kike fushi?" Yayi tambayar kansa tsaye yana tsareta da idanu. Da sauri ta daga kanta sai kuma ta sauke,batason ko yaya ta bashi qofar karantarta,don haka ta tattara dukka qwarin gwiwarta tace. "Fushi?....." "Karki qaryata.....kada ki musa,na gani a idanunki" Ya furta can qasa yana sake dafata da idanunsan nan masu tarin dafi da wani magnet me qarfin gaske. "Ba zaki iya kokawa da abinda yake cikin zuciyarki ba.....amma idan zaki iya na baki dama" Ya fada yana miqewa tsam yana gyara daurin agogon hannunsa. "Gobe zakiyi baqi" Maganansa na yanzun ya sakata daga kanta badon ta shirya ba,sai shima akayi sa'a idanuwanta yake kalla. "Mama na.....mamana zatazo" Idanun ta sauke qasa a hankali. Sai taji wani abu me nauyi yana ratsata,wani yanayi da ya saukar mata da tsananin kewar mahaifiyarta lokaci daya. Ashe yana da uwa?,yana da mahaifiya?. Haka kawai saita samu kanta da son ganin mamarshi,idanu da zuciyarta suka shiga wassafa mata yadda take a cikin tunani da hasashenta. "Ba wani abu.....bakya buqatar komai?" Ta tsinci muryarsa dab da ita. Kadan ta motsa baya tana lumshe idanunta bugun zuciyarta yana son canzawa. Kai ta girgiza masa,saidai har lokacin tana jin alamunsa a kusa da ita,har lokacin bataji alamun ya janye ba "Goodnight" Taji ya furta a hankali da yaren France da yake sake fusgar hankalinta dashi. Bata iya bude idanunta ba har sai data daina jin alamunsa. Ta waresu a hankali tana sauke dubanta akan hanyar daya wuce din. Zuciyarta ta matse kadan sanda take raya mata ya fita.....ya fita daga gidan,wani fili taji zuciyarta tayi,wani sarari da zuciyartata take raya mata kamar akwai wani abu da yayi nesa da zuciyarta. Abubuwansa da yawa mamaki suke bata......amma irin wannan abinda yake matan.....baya masa nauyi?,bayajin kamar be kyauta ba?. Wa zata kira tayi maganan dashi?. "Falaak" Wata zuciyar ta gaya mata. Shuru tayi tana juya abun a ranta "Eh falaak.....itace ta biyo ta hanyar" Zuciyarta ta sake jadda mata. Amma ta yaya zatayi irin wannan maganan da falaak din?. "Ita kadai ce zata fahimta" Wani sashe na zuciyarta ya sake bata amsa. Wayarta ta jawo,ta bude watsapp dinta da takan kwana biyu bata hau ba. Wancan satin kaman taga saqon falaak din ta watsapp ta sabuwar number da bata tsaya tantance code din wacce qasar bane,tayi copying number din ta dawo wajen kira ta dora number din sannan ta kirata. Tayita ringing ba'a dauka ba,sai dab da zata katse sannan taji an dauka,saidai maimakon muryar falaak ita kadai,sai muryoyinsu a cakude ita da maleek da suka fara shiga kunnenta. (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) Cikin shagwaba take masa magana shi kuma ya lalace yana rarrashinta. Gaban akhnan ya tsinke ya fadi,ba shiri ta kashe wayar. Kunnuwanta ba zasu iya jin abinda suke fada ba,maganganu ne masu nauyi sosai,da alama ma batasanma ta daga wayar ba gaba daya. Jefar da wayar tayi gefe tana jan siririn tsaki,yaushe falaak ta lalace haka ne?. Yaushe falaak ta koma haka?. Ba doguwar mu'amala bace a tsakaninsu......amma ta sani ba haka halinta yake ba. Ta lumshe idanunta ta budesu a hankali,ya tafi ya barta da qamshinsa,ya tafi ya bar mata memories masu yawa a tare dashi. "Girmama na gaba.....girmama baqo" Ta tuna daya daga cikin lesson data dauka a zamanta cikin gidan. Ta bude idanunta a hankali,dole kenan tayi practicing daya daga cikin abinda ta koya kodon ta samu a kammala wannan zaman waqafin na rules din rayuwar masarautar da har yanzu ita batasan a wanne matsayi take ba. ~Ta cikin motar da yake tafiya idanunsa zube kan hasken farin watan daya haske sararin samaniya. Baisan murmushi yakeyi ba,baisan murmushi bane akan fuskarsa ba sai da yakai hannu ya shafa fuskarsa a hankali. Ya tsinci abubuwa da yawa da baiyi zatonsa ba tattare da ita. Quruciya.....zallar quruciya take gwadawa da suka sanya ya sake raina shekarunta. Iya yadda takeyi kawai ya tabbatar masa quruciya ta mata yawa,kuma ba kowa zai.gane hakan ba sai wanda zama ya hadasu kaman hakan. Kwarjini kawai takewa mutane.....wannan izzar da sarautar dake jikinta mutane ke mata kallon girma da manyance. "Da gaske batasan komai ba?" Ya sake tambayar kansa da kansa cike da mamaki still. Inda ace ya aureta ne kawai fa don sha'awa?,inda ace ya aureta ne don ya biya buqatar ransa a kanta fa?. Lallai inda hakanne da babbar matsala za'a samu. Ya lumshe idonsa yana tuna yanayin data sanyashi,ya sake murmusawa a hankali kaman wanda ya samu tabin qwaqwalwa. Tunda yazo duniya bai tana jin yanayi irin wannan ba,ko shi yasa maleek yace sun dade a matsayin buhunhuna kuma bahuna?,akwai abinda maleek yaji kenan sama da abinda yaji a nasa jikin?. Iya tambayar kawai ta saukar masa da wani tashin tsigar jiki,kwanyarsa da zuciyarsa suka fara masa hasashen can inda maleek yaje,sai yaji kawai ya kasa zama shi kadai,ya jawo pillow din dake cikin motar ya sakashi a qirjinsa yana jin yadda mararsa take qullewa sosai. Bai iya sake bude idanunsa ba sai sanda motocinsa suka sauka cikin masarautar aba jifar. Kowa ya tsaya suna jiran motar da yake ciki ta bude kanta da kanta. A nutse ya ajiye pillow din,ya zura qafafunsa qasa a hankali,kyakkyawan takalminsa qirar qasar italy ya fara fitowa,sannan gangar jikinsa yana sabe da 'yar saman suit dinsa. Jikinsa a mace yake gaba daya,yayi wani laushi sosai,amma hakan bai boye kwarjininsa ba ko kadan. Kaman kullum,duk inda ya taka hadimai ne da bayi suke zubewa suna gaidashi da girmamawa. Sashen nanay ya nufa,don qa'idarsa ne kome dare idan ya fita ya dawo sai yaje ya ganta,ballantana yanzun daya dauki kwanaki biyar ba tare daya sanyata a idanunsa ba. Ciki lafiyayyen parlor din dake da girma da yalwa,cikin wani yanayi na kayan qawa da suke nuna zallar isa qasaita da qarfin ikon da masarautar oromo ke dashi. Iyalin khadeeja yunnus jallata ne zaune a ciki,cikin wani yanayi na walwala qauna da fahimtar juna. Balqees,khansaaa,rumaisa,Aaanani,sai auta noorah wadda ke zaune gefe daban da camera dinta a hannu da alama wasu hotuna take dubawa. Kaya ne fal a gabansu suna shiryasu cikin wasu irin abubuwa masu kama da akwati,suna yi suna hira cikin harshe da yaren oromo. Sallamarsa ta sanyasu tsagaita hirar tasu,cikin girmamawa da qaunar juna a tsakaninsu ya qara so suna masa sannu da zuwa. A girmame ya gaida balqees da hasnaaa,sannan sauran suka gaidashi,noorah na maqale da hannunsa tana qoqarin nuna masa hotunan data dauka. Hannu yasa da murmushi ya karbi camera din yana kallon hotunan,hotunane na wasu kyawawan tsuntsaye da shi kansa sai daya tsaya yana kallonsu. Hannu yasa yayi zooming hoton da kyau,harda aku.....dawisun da yasan bata dashi a baya cikin tsuntsayenta,ga wasu tattabaru da suka burgeshi sosai. "Yaushe akayi wannan auta?" Ya tambayeta da murmushi kan fuskarsa yana waiwayawa gefansa inda take tsaye. Murmushi itama ta saki daya qara bayyanar da kyan yarinyar,taji dadi sosai yadda obbo dinta idanunsa suka nuna burgewar da kayan sukayi masa. *zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 08187255862 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 08187255862 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 58* "Wancan satin da baka nan obbo" "Ma sha Allah,Allahumma bareek,daga ina kika siyosu?" "Nigeria" Ta fada qasa qasa,yadda tayi maganan kuma ya bawa kowa dariya a parlor din. Ya fidda manyan idanunsa waje. "Nigeria kuma?" Kai ta jinjina tana dariya. "Eh obbo,a HALY JASHERU VENTURES(07046665338)obbo......harda kaji tana siyarwa fa,masu kyau sosai obbo,zaka iyayin ado dasu......" Kai yake jinjinawa,yana mamakin qaunarta da tsuntsaye sosai,gari ya gari har Nigeria?. "Taya kuka hadu noorah?" Balqees dake zaune riqe da habarta ta fada tana duban noorah din da mamaki. Siririyar dariyar data bayyana quruciyarta tayi tana sake riqe hannun haisam. "Tana zuwa nan qasar sarin pure mayukan zaitun,hulba,habbatussauda da man kwakwa dama sauran ire irensu". Kai ya jinjina sosai yana murmushi. Mutum ne shi da yakeso yaga dan adam me dogaro da kansa,zuciyarsa bata mutu ba sam,kuma duk cikin 'yan uwansa,tarin dukiya da mulki da suke ciki ba wanda baya juya business dinsa hatta da Aareef da yake bin noorah "Ma sha Allah.....zan qara jari da alama a siya tattabaru,nima a kawomin dawisu da aku guda daya" Wani tsalle tayi tana d'aneshi,farinciki yana cikata, "Na gode obbo na gode" Ta fada da harshen oromo farinciki yana cikata. Tabe baki Aanani tayi,itakam haushi takeji idan noorah ta zauna tana bayanin riba da ake samu akan tsuntsayen. "Kome yake cikin siyan wadannan dabbobin oho". Da sauri hasnaa ta juyo yana duban Aanani. "Sirri ne....noorah ta fiku wayo,bansan ya akayi tasan abinda ake samu cikin kasuwancinsu ba.....riba ce ba qarama ba,ina kyautata zaton nan gaba kadan cikin mata na gidannan itace me arziqinmu" Maganan kusan ya saka kowa dariya,duk da suna lura da kusan hakanne abinda hasnaaa ta fada. Tsautsayi shine abinda ya fito da ita daga daki. Zaman dakin a kwanakin ya fiye mata komai,ya fiye mata fitowa ta zauna a cikinsu,daga sanda ta fahimci tarin walwalar da suke ciki saboda auren captain sheikh,daga sannan ta sanyawa ranta nisantarsu dama zama a cikinsu. Ba yadda za'a zauna a tashi ba tare da sunyi wata magana data danganci matarsa da aurensa ba. Ba yadda za'a zauna lafiya ba tare da an tabo batun aurensa ba,saita zabi ta yita kwanciya cikin daki da sunan jikinta ne har yanzu baiyi qwari ba. Ruwa take nema Don haka dole ta fito nan din,don freezer dinsu an fiddasu duka za'a sanya sabo,kuma basu qaraso ba har yanzu. A hankali take takowa,sosai duk wanda ya kalleta zaiga ramar da tayi. Tana jin kamar iska tana yawo da ita cikin sararin samaniya ne kawai. Muryarsa taji sanda yake fadin. "Nanay fa?". Kalma daya ce tak amma tasirinta a zuciyarta me girma da fadi ne. Sautinsa da muryarsa wani abu ne da har yanzu tasha kwatantata data sauran maza amma ba wanda ya dace tasa tayi daidai da tata a mizani. Kaman ta juya ta koma saboda tsananin bugawar da zuciyarta takeyi amma saita kasa. Tayi kewarsa sosai,tana kuma buqatar ganin wannan kyakkyawan kamilalliyar fuskar dake da wani irin kamewa da nutsuwa. Da sallama ta shiga,idanunta kuma a kansa. Sun amsa duka,amma shi kyawawan labbansa ne kawai taga sunyi motsi. Waigowa yayo shima kaman sauran mutanen cikin parlor din,sai da numfashinta ya kusa qwacewa na wucin gadi. Wani kyau.....zallar kyau taga yayi mata duk da ya cire suit din saman sai T-shirt din cikin. Bata sani ba.....ko don ganinsa cikin qananun kaya wani baqon abune a tare dashi shi yasa?. Idanunta ta lumshe zuciyarta na tsananin bugawa a qirjinta. "Sannu saamee.....kin fito?" Balqees ta tambaya tana kallon idanunta. Kai ta daga a hankali ta motsa labbanta tana amsawa da "Eh" Sannan ta daga idanunta tana zubewa akan fuskarsa. Ba ita yake kalla ba,still hankalisa yana kan camera din noorah yana ci gaba da kallon tsuntsayen da yaji sun burgeshi sosai. Lafiyayyu dasu da irin salon kiwon daya tabbatar sun samu kulawa. "Barka da dare,ina yini" Ta fada da yaren oromo. Kansa ya daga yadan kalleta. "Lafiya lau malama.....ya jikin naki?" "Alhmdlh da sauqi" Ta bashi amsa wani abu yayi mata tsaye. General kulawa ce normal yadda ya saba. Yadda ya saba yiwa su noorah Aanani da rumaisa,harma sai taga kaman yafi nuna musu kulawa akan yadda yake nuna matan. "Allah yasa kaffara" Ya fada yana miqawa noorah camera dinta. "Nanay ta kwanta ko?" Kai noorah ta daga masa. "Tun dazun,tace tanaso gobe ta tashi da wuri...." "Nanay ta rasa sukuni fa,kaman gobe ba zatazo ba,tace surukarta kawai takeson gani......anya kwanan nan ba zaka rasa matsayinka gurin nanay ba?" Murmushi ya saki kadan yana jin jikinsa har yanzu ba qwari,murarsa kaman tanason yin gana,still mararsa a daure take har yanzun kaman tanason masa ciwon data saba lokaci lokaci. (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) "Banajin akwai me iya qwace wannan". "Saini" Muryar hussam ta cika parlor din sanda yake shigowa hannunsa dauke da mangwaro da aka yanka. Harara ya juya ya watsa masa,hakan ya sanya hussam shiga taitayinsa,yadan koma da baya yayo sallama sannan ya shigo,kai tsaye kuma ya wuce kusa da Aanani zai zauna. "Tashi" Haisam yace dashi kai tsaye. Shi da Aanani dukkansu ba haquri,abokin rigimarta ne sosai,kaman ba rumaisa bace sakuwarsa Aanani ce. Yayi narai narai da idanu yana sauya gurin zama,saidai ko sakewa haisam bai bari yayi ba yace masa. "Ina report na ma'aikatan kamfanin can na dubai?". Idanu ya narke,bai taba ganin mutumin da baya gajiya da sabga ba irin haisam din. "Obbo.....an kammala komai,kawai na d'aga qafa ne a gama biki sannan" "Ni nace maka?" Ya fadi kansa tsaye idanunnan nasa na cikin na hussam. "Kayi haquri......hukuma ta bamu sha biyar ga sabon wata zamu iya bude kamfanin mu" "Alhamdulillah" Ya fada a hankali ya miqa hannu yana karbar wayar hussam din da yake miqa masa. Hotuna ne na dukka sassan kamfanin,kamfanin da haka kawai ya shiga ransa saboda yawan abokan hulda na kasuwanci da suke dasu a qasar Dubai din. Haka kawai yaji a ransa wannan karon hussam yayi abun arziqin da bai taba yin irinsa ba,ya daga kai ya dubi hussam din dake bada labarin shima ya hada tasa walimar. "Inde da shashashanci a ciki ka tabbatar ba za'a yita ba" "Aah obbo....walima fa,ba party bane wannan na rantse" Idanunsa kawai ya maida kan wayar,sai baice komai ba yaci gaba da kallon hotunan. Yana ji a ransa ya kamata kawai yasa hussam ya fidda mata yayi masa aure,kaman hankalinsa sai yafi haka nutsuwa. Duk da ba wani shashashanci yake ba....jinin aba jifar dukka Allah ya shirya masa,kawai rawar kansa wani lokaci ke sanyawa basa shiri da haisam. Yana da tara abokai kala kala,hakan kuma baiwa haisam din ba,don yana iya kawo matsalar tarbiyya. Da qyar takai kanta kitchen din tana ci gaba da sauraren maganganu da hirarrakinsu. Gaba daya sai yanzu take jin kanta lallai ita bare ce,lallai ita din wata dabance da babu wanda ya damu da ita. "Zanje nima.....tabbas zanje" Ta fadawa kanta tana qoqarin hadiye abinda yake taso mata. A yanzun ta shirya fuskantar matar haisam.....ta shirya tsaiwa taga wacece ita?,ta kuma shirya karbar haisam din koda dadi ko bata dadi ba.......zata gwada mata itace bare.....zata gwada mata itace ta shigo rayuwarsu.....itace ta fado muhallin daba nata ba. "Sha biyar ga wata.....wata daya kenan a gaba?" Ta tambayi kanta. "Lallai ne a wannan lokacin bikin aure zai hade dana bude kamfani" Ta fadi can qasan ranta,saima ta fasa daukan ruwan,ta fito tana ficewa,wanda harta fice dimma basu kula da ita ba saboda hirarrakinsu da sukeyi,amma ta lura haisam din baya gurin da alama shi ya fice ne. *_W A S H E G A R I_* Cikin girma isa da qasaita jerin motocin masarautar aba jifar ke shigewa gate din palace learning residence wanda ke dauke da wata fakadediyar harabar da zata cinye dukka adadin motocin da zasu shigo cikinta ba tare da sun takura ba. Wani abu me sanyi nanay keji yana ratsata tunda suka shigo farfajiyar gidan. Wani zumudi ne yake kamata da zaquwar data kwana da ita tun a daren jiya. Daga jiya zuwa yau ta rufe idanunta tayi addu'a cikin zuciyarta har batasan adadi ba. Tana roqon Allah yadda ya tanqwara zuciyarta ya bata ikon daidaita adalci tsakanin 'ya'yanta,soyayyar dayansu bai sanya ta fifitashi a gaban idanunsu ba.....Allah ya bata ikon yin adalci tsakanin surukanta da duk za'a auro mata.. Batasan me yasa ba.....ko don haisam din na dabanne a ranta shi yasa komai nasa.....komai daya shafeshi yake zama na daban a ranta?. Tayi bismillah tana sako qafafunta waje sanda haisam ya bude mata motar da take ciki,hadiman da suke tare da ita suka matso don gyara mata rigarta ta baya,ya daga musu hannu yana dakatar dasu. Ba gwanar fita bace nanay sam,zai wahala ace maka yau bata nan,amma duk sanda zata fita din haisam ke hidimar rakata yana kula da lafiyarta da motsinta har su dawo. Shi ya matsa da kansa ta bayanta ya gyara mata komai,idanun samee dake cikinsu Aaanani yana kansa. Wani sake burgeta yakeyi,tana ji har cikin zuciyarta ba zatayi asarar wannan ba,shi din mallakinta ne. Tana ji a ranta inama ace itace tsaye haka a gabansa yake hidima da ita?. Jerawa sukayi shi da Nanay din suna takawa a hankali,su rumaisa na bayansu,hadimanta mata a bayansu rumaisa din,sai guards da dogaran da suke cikin fararen kaya da suka cika gida kaca kaca sama da yadda yake a baya. *zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 08187255862 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 08187255862 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 59* Cikin kamalar nan tata,uwa mabada maama khadeeja yunnus jallata......baya goya marayu,tayi tata tayi ta saura,uwar tausayi da taimako,MAMA OROMO kaman yadda da dama jama'anta ke kiranta take takawa zuwa cikin gidan,hannunta cikin na haisam yana riqe da ita. Wani kalan kwantaccen murmushi ne akan fuskarta,murmushin da iyashi kadai ya isa ya gaya maka labarin dake cikin zuciyarta. Sanye take da wani lallausan tufafi daya kasance ainihin suturar qabilar oromo,saidai dinkin da aka mata dinki ne dake nuna sarauta da kuma girma irin da dattijantaka. Cikin parlor na biyu suka yada zango,yayi tsaye riqe da hannun nanay,daidai sanda hadiman gidan sarautar aba jifar sanye da fararen kaya suka fara shigowa da wasu akwatuna,wanda shi kansa baisan sanda suka taho dasu ba. Wasu irin akwati ne,4corner me masifar daukar idanu,wanda baka da tabbacin da meye aka tsarashi,off white ne da aka yiwa adon royal gold a jiki. Idanunsa ya lumshe a hankali ya bude yana azasu kan nanay. Baisan wacce irin qauna takewa akhnan ba tun yanzu?. Wadannan akwatuna ne masu tsananin tsada da daraja,wadanda suka kusa guda ashirin da hudu,iya akwatin kawai baisan ma meye a ciki ba. Murmushi ta sakar masa a tausashe,tasan abinda ke kai kawo a ransa,tasan meye a zuciyarsa. Iya hussam da yaga kayan sai daya fara qorafi. "Iyyeee......matar d'an lele,anya zamu samu sauran space kuwa nanay?" Murmushi kawai tayi tana girgiza kanta. Ta sani bawai hussam ya fadi bane har zuciyarsa,yana da wasa da barkwanci,amma da gaske haisam daban yake a zuciyarta,dole ko meye yazo daga gareshi ya zama na daban. "Zamuje ganin d'iyata goben....." "Banda ni nanay,kinsan halinsa ko,zaice ne zamuje kalle masa mata,daidai sa Aareef Allah yasa ya barshi,idan ta fito zamu hadu a nan,Allah ya dawo daku lafiya,gobenma inajin zanje addis ababa jibi zan dawo" Dariya ya sake bata,yasan halin yayanshi kaf.....amma wani lokaci tsabar wasa da ya yiwa hussam yawa ne yasa basa shiri da haisam din. Dukkaninsu kowa ya samu guri ya zauna,hakanan duk hadiman dake cikin gidan suka qaraso cikin matuqar ladabi da girmamawar nan da suka saba da ita suka diban gaisuwa. Cikin mintina qalilan suka cika gabansu da abubuwan ciye ciye,zenabu taja baya kanta a qasa tace. "Wannan aike ne daga uwargijiya,tana ciki yanzun nan zata fito,tace ayi mata afuwa da rashin kammala shirinta kafin isowarki mama oromo.....yanayin shigar ne yasha banban da tasu" Murmushi nanay tayi,tana sake dafe hannun haisam da har yanzu yake cikin nata,saidai kafin tace komai haisam din ya rigata magana. "Ki gaya mata zamu shigo ciki nida nanay mu sameta" "In sha Allah" Zenabu ta furta ta miqe tana shaidawa bara'atu,ta tattaka itama tana komawa ciki. Tsaye kawai tayi gaban babbab madubin,tana kallon zaman doguwar rigar da aka dinkata daga asalin yadin alharir na asali me tsadar gaske. Ko ba'a gaya mata ba kayan ta sani sun nuna alaman kaya ne masu dadadden tarihi,bawai saboda tsufa ba.....aaha,hasalima kayan kaya ne masu madaukakiyar darajar da idan za'a kaisu kasuwa yanzu tabbas za'a bada kudade masu nauyi sa dimbin yawa a kansu kafin a karbesu. Kawai ta fahimci tsohon yadin alharir ne kasancewarta me mu'amala da yaduka zararruka auduga da dukkan wani yadi me tsada,fara gudanar da kamfaninta na sahel couture ya sanya take iya fahimtar abubuwa da dama dangane da suturu na alfarma masu daraja. Abu na biyu kayan sai taga suna mata kama da wata sutura,wani tufafi da ta taba ganin kamar cikin kayan da momma ta bata.....a jikin wata kaman ranar aurenta data gaza tuna wacece?. Ta sake kallon sarqar wuyanta dama bracelet din hannunta,duka abu guda yake gwada mata. "Ga wannan......itace kyautar da zaki miqa mata bayan kun gaisa" Birra ta fada tana miqawa akhnan wani nannadadden abu me qyalli,shiba paper ba shi ba leda ba. Juyashi take kawai cikin hannunta,kafin ta dago tana duban birra. "Birra.....me yasa duka wannan......me yake faruwa?,zuciyata kamar tana fadamin akwai wani abu" Qasa birra tayi da kanta,tana jin zuciyarta na mata nauyi kadan. "Babu komai.....babu komai ranki ya dade sai alkhairi" Kafin ta sake cewa komai bara'atu ta shigo,ta kuma isar da saqon haisam. "Ki shiga dasu duk inda suka zabi shiga" Ta fadi tana sake maida dubanta kan madubi. Kayan sun mata kyau,shigar ta mata kyau sosai ita kanta ta gani,hakanan kayan cif cif jikinta kamar don ita aka dinkasu. Ta lumshe idanunta sannan ta budesu a hankali,tana jin zuciyarta na wani irin motsawa kamar akwai wani abu daya tabata. "Mu qarasa ciki nanay.....akwai kyautar da nakeso nayi miki,ina fata kuma ta zama kyauta mafi karbuwa a gurinki da bazaki manta da ita ba" Murmushi tayi a hankali ta soma takawa tare dashi,ta amsa masa a hankali saboda ita kanta tana jin wani yanayi a zuciyarta da gangar jikinta "Bayan wannan kyautar da kayimin na suruka sukutum da guda?,harda wata kyautar ta daban muhammad?" Kai ya gyada mata a hankali "Akwai nanay.....akwai saura" Jinjina kai itama tayi. "To na gode,Allah yayi maka albarka" "Ameen" Ya amsa yana jin wani sanyi cikin ransa. Addu'arta ta daban ce a gurinsa,ba wani abu a duniya ke masa dadi sama da yadda addu'arta ke masa. Qawataccen parlor ne wanda yasha banban da sauran falukan gidan,tunda tazo gidanma ba'a taba budeshi ba bare a shiga,iyakaci a gyarashi a tsaftaceshi. Bismillah nanay tayi ta zauna saman tattausan kujerar data lume a ciki. Dubansa tayi sanda taga yana shirin zama kusa da ita. "Ya haka?" "Nanay?" Ya furta a hankali. "Jeka da kanka ka tahomin da ita,jeka da kanka ka taho da matarka" Murmusawa yayi,sannan ya miqe a hankali yana takawa. Hakan yakeso,zaiso hakan sosai,amma yake alkunyawa nanay. Zuciyarsa a matse take da wani abu da yafi masa kama da zumudi. Daren jiya da qyar yayi wani wahalallen bacci da bai taba wahala irinsa ba. Ciwon mara sosai yayi shi kadai cikin sassansa. Yasha kanwa yasha lemon tsami har doze din yaso ya wuce,sai gab da asuba ya samu sassauci,don bai farka ba sai bayan an kammala sallar asuba da wasu mintuna,jikinsa sharkaf da gumi da janaba,yayi wanka a daddafe yayi sallar sannan ya koma ya kwanta yana jin marar har yanzu a daure,hakanan ba wani kuzari a jikinsa sam. Ta bawa qofa baya,tana tsaye har yanzu gaban madubin,wannan ya bashi daman fara arba da wadannan blue eyes din nata da haskensu yake cika masa idanu. Fes komai ya dawo kanta,abinda ya faru tsakaninsu jiya. Wata irin kunya ta kamata har taji kaman qafafunta sun soma rawa. "Ya ilaheee......ya rahman" Ya furta can qasan maqoshinsa yana hadiyar wani abu,adam apple dinsa daya fito sosai kaman zaka sanya hannu ka ciroshi ya motsa sama da qasa. Ta zare nata idanun daga kansa,don bata da juriyar kallonsa tun daga jiya da abinda ya mata ya zarta na wadancan kwanakin,tayi qasa da kanta kawai tana murza bracelet din hannunta tana jinta kamar tana nutsewa a qasa. Idanunsa ya lumshe sanda ya iso gabanta,numfashinsa yana masa wani irin nauyi,yana jin kamar akwai wani abu dake fusgar zuciyarsa. Saidai duk yadda yakeji bugawar da tata zuciyar takeyi ta danne tashi. Wani irin salon dressing take gani a jikinsa karo ma farko tunda ta fara ganinsa,ya fito sak MATASHIN OROMO da shigar kayansu na al'ada da aka zamanantar dasu. Kayan sun bala'in kwanta masa sunyi biyayya tamkar sunsan a jikin wanda suke. Hannunsa ya miqa zai riqe hannuwanta da bracelet din suka zauna mata tamkar dama can mallakinta ne,amma daya tuna nanay nacan zaune tana jiransu sai ya janye hannun nasa da sauri. Ya sani,zai wahala ya tabata ya iya jurewa wani abu bai biyo baya ba,bayason kuma yanayinsa ya sauya kwata kwata,don yasan tsaf nanay zata dago wani abu. "Barka da warhaka" Ta samu kanta da fadi tana rusunar da kanta da alama ta girmamawa. Idanu ya zuba mata,karon farko da yaji tayi wani irin burgeshi,yanayin gaisuwar ya mata kyau,cakude da izza da quruciyarta da yake gani muraran tun daga jiya.. (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) Gaisuwarta tayi,cikin yanayin dake nuna tarbiyyar masarauta da qabilar oromo ta fara shigarta. Saidai shi ko kadan baya ra'ayin irin wannan gaisuwar,ba irinta yakeso ba. Ya jima da tsara rayuwarsa da dukkan macen da Allah ya qaddara zai aura. Koda da gaisuwa yana fadin zata zama ta musamman ne. "Kinyimin kyau sosai princess of agadez......na jawoki kusa ki kiramin bappi" Ya furta muryarsa a narke yana karya wuyansa idanunsa na narkewa a kanta,kamar ya manta gaban wa yake. Har cikin b'argonta taji wannan muryar......wannan husky voice din nasa da yayi wani irin laushi da taushi,cikin nutsatsen sautin da kamar zabarsu yayi ya kuma jerasu kafin ya furta mata su. Shi kansa baisan me yakeji ba....baisan me yake fusgarsa a kanta ba....baiji kuma yanason ya dauke kallonsa daga kanta ba. Wani yanayi ne me cakude da tausayi,tausayin batasan ainihin suturar wadda take sanye da ita ba.....suturar wata sashe na jikinta.....suturar halitta mafi qaunarta a duniya,suturar halitta mafi soyuwa a gareta a duniya. Qasa ta sakeyi da kanta tana sake murza bracelet din. A hankali idanunta suka sauka kan qafarsa,wannan qafar dake mata wani irin kyau,wannan qafar dake burgeta cikin baqin takalmin daya fito da zara zaran yatsunsa ya kuma haska farar fatar qafar tasa dake kwance lumui kaman batasan wani abu wai qasa ko qura ba. Batasan me yasa komai ta kalla yake burgeta a tattare dashi ba......batasan me yasa komai nasa yake jan hankalinta ba,komai nasa kaman ya zaba kaman ya tsara,har wani lokaci sai taji zuciyarta tana gaya mata,ya fiki kaza.....ya fiki kaza. Tafin hannunsa ya sanya qarqashin idanunta yana bude mata su,ta dora idonta a nutse akai. Wani guri da a koyaushe take samun nutsuwa koda a rude take muddin zai cakuda zara zaran yatsun hannunsa da nata. Tana jin wani lokacin idan yayi hakan,kamar wani assurance yake bata na samun nutsuwa. "Zamu iya tafiya?" Ya fada da French din nan nasa me cike da wani accent da take yawan gwadawa ko zata iya magana dashi. "Inaso a sanda idanun nanay ke kallonmu......ta kallemu a matsayin cikakkun ma'aurata,wadanda basu da matsalan komai.....ma'auratan da sukayi auren qauna da soyayya......ba wadanda sukayi auren yarjejeniya ba" Yayi maganan ne cike da tarin nutsuwar nan dake masa ado,amma sai kalmarsa ta qarshe ta haifar mata da wani faduwar gaba. "Auren yarjejeniya.....na manta" Ta fada can qasan ranta. Har yanzu yana riqe kenan da maganganun mammina?,har yanzu kenan yana kan alqawarin mammina?....hakan yana nufin?" Sai zaren tunanin nata ya tsinke tana jin wata fargaba. "Hakan yana nufin wataran.....komai zai qare?" Tambayar da bata lalubo amsarta ba,ta tsinci wannan lallausan tafin hannun nasa cikin nata. Wani space ya bata nayin shuru saboda heart rate dinta ya daidaita. "Kin shirya?" Ya fadi a hankali. Bata ja da nisa ba kawai ta daga masa kai. Batason kowa yaga sun dade a cikin dakin da daga ita saishi ballanta a zargi wani abu,ya jinjina kansa a hankali ya soma takawa tana biye dashi. Qarar taba qofar ya sanya nanay maido hankalinta ga hanya maimakon TV din daketa aiki ba wanda ke zama ya kalla,wanda suke hasko labaran qasa na yammaci a gidan tv mallakin gwamnatin qasar Ethiopia din. Da farko haisam ta fara kalla,sannan a hankali ta aje idanunta akan fuskar akhnan. Wani irin abu me qarfin gaske ne ya fusgeta,wani irin yanayi da yafi kama dana Mitumin da aka tasa a bacci ba tare daya shirya ba. Idanu sosai ta zubawa akhnan din,wani irin abu take gani yana gilmawa akan fuskar ta,wasu kamanni na sak da sak......kamannin da suke cikin dukkanin baccinta na shekara da shekaru. Da fari qafafunta da hannayenta ne sukayi wani irin sanyi,don kamannin da take gani yanzu a gabanta ta sani wani abune me wahalar kasancewa. To amma koda ta matso kusa da ita....koda ta zubawa shigarta idanu sai take ganin safeena a gabanta,safeena cikin shigar kayan aurenta Randa za'a kaita gidan ajani......safeena da quruciyarta ta sake dawowa baya kaman wadancan shekarun da suke lokacin 'yammatancinsu. "Ki nutsu Khadija......wannan din surukarki ce,kada ki koma maganan badini zahiri ne a gabanki" Wannan tunasarwar da zuciyarta tayi mata shine abinda ya sanyata miqewa. Idanunta fes akan Fuskar akhnan data sunkuyar da ita qasa kadan. Wani irin nauyi taji tana ji daga kallon fuskar matar sau daya tak. Wani irin kwarjini taji tayi mata matuqa da gaske,kwarjinin da taji zuciyarta a take tana gaya mata. *zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 08187255862 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 08187255862 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 60* "Ga asalin inda kwarjininsa ya samo asali da alama". Kallo daya tayi mata,amma sai take ganin wani yanayi tattare da matar. Nutsuwa kamala da cikakkiyar haiba,ga wata irin kunya da batasan abinda ya kawota ba,kalan kunya da bata taba jinta dangane da wani dan adam ba. "Ma sha Allah,tabarakarrahman" Nanay ta gaza jurewa sai data furta. Duk da akwai wasu kamanni saman fuskar akhnan din da take hange yanzu haka......amma hakan bai gaza banbanta wannan kyan da wancan kyan ba,wasu banbance babance da tana sake qarasowa gabanta tana ganinsu. Hannuwanta dukka biyun ta miqa akhnan din tana dubanta da wani irin tarin qauna da takeji ya saukar mata,qaunar da ta ninka wadda takeji kafin takai ga ganinta. "Bismillahir rahmanir rahim......ina miki maraba da shigowa cikinmu,ina miki maraba da shigowa masarautar oromo.....ina miki kuma maraba da shigowa ahalin aba jifar" Tayi maganan dukka tana miqawa akhnan hannunta. Ji tayi ba zata iya ci gaba da tsaiwa a gabanta ba,karon farko data rusunawa wani dan adam akan gwiwoyinta bayan sultane dinta,saita fara sulalewa zatakai qasa,abinda ya dauki hankalin haisam matuqa da gaske d wanin irin yanayi na burgewa da mamaki,saidai amma caraf nanay ta kama hannuwan nata tana fadin. "A'ah.....ke a gareni diyace,tamkar dai Aanani noorah rumaisa balqees hasnaaa husssss......." Sai maganan Nanay ya datse daga sunayen da take jero mata sakamakon sauka da idanunta sukayi akan abun hannun akhnan din. Cak komai ya tsaya mata.....kwanyarta ta kwasheta da wani irin gudu tana maidata shekarun baya. Shekarun da safeena ta kawo mata ajiyar wannan abun hannun. "Ki ajiyemin,kinfi safiyya iya adani,Ahmad ne ya bani,haka kawai nakw tsoron ajiyarsa cikin gidan" Ta ajiyeshi da matuqar muhimmanci,saidai safeena ta karba daga baya tana shaida mata yanzun ta samu tabbacin zata iya ajiyarshi. "A......a ina kika samoshi?" Ta furta idanunta a waje tana dan girgiza hannun akhnan da sauri. Da hanzari akhnan ta daga kai gabanta yana faduwa,tanaso ta gane akan me dattijuwar ke magana,saita fuskanci idanunta da hankalinta suna kan abun hannun ta. Da sauri ta daga kai tana kallon haisam,gabanta yana tsananta faduwa,tunani kala kala yana sarqa kanshi da kanshi a zuciyarta,ina ya samo ya bata?. "Nine na bata" Ya fada calmly bayan ya zare idanunsa daga kan akhnan dake masa kallon da ya gama fassarashi,ya kuma tafi kai tsaye zuwa ga ma'anar kallon dake cikin zuciyarta. Still nanay bata saki hannun akhnan ba,ta maida dubanata ga haisam a rikice. "Nine na bata nanay,nace ta saka don ki sake gamsuwa da gaske ita din jinin SAFEENA ce". Maganan ya saukowa nanay da wani mugun nauyi,har sai da tayi taga taga kaman zata fadi,saidai kafin yakai ga qarasowa gurin tuni akhnan ta sanya siraran yatsunta ta taro bayanta sosai,yana qarasowa sai ya tallafeta ta hanyar tsaiwa ta bayan nata. "Baka tabamin irin wannan wasan ba" Ta fada tana maida Fuskarta da dukka idanunta akan abun hannun akhnan. "Baka qarya muhammad,baka tabamin qarya ba....kuma a yanzun ma nasan ba zaka fara ba,ba halinka bace" Ta qara fadi tana sakin hannayen akhnan. Tafukan hannayenta dukka biyun ta sanya tsakanin gefe da gefe na fuskar akhnan,ta juya fuskar tata daga hagu zuwa dama,ta saketa,ta kama gefan mayafin dake lullube a kanta ta murza,sai ta sake saki tana sake kamo hannuwan akhnan din. Yatsunta ta kalla dogaye wadanda har yanzu da sauran jan lallen da yayi dishi dishi,sai ta juya tafin hannunta tana qare musu kallo da kyau. Ba wanda ya zata a cikin su shi da ita,sai wata wawar runguma kawai da sukaga ta kaiwa akhnan din tana fashewa da kuka mara sauti,saidai muryarta ta nuna kukan takeyi "Allahu akhbar......Allah akhbar,Allahumma lakal hamdu kulluh,wa lakashshukr kulluh.... Lallai ba shakka ke din jinin SAFEENA ce,tsatson safeena ce ke" Ta qarasa fada dukka jikinta yana girgiza da alamar abune me zurfi da taba rai. Bata gane komai ba har sanda haisam ya kama nanay ta tayashi suka zauna. Banda sunan safeena data fahimta a dukka maganganunta,safeena mahaifiyarta bata gane komai ba,ta zuba ma nanay dake riqe da hannunta har yanzu idanu,sannan ta maida idanun nata ga haisam dake matsa hannun nanay din a hankali cikin wani yanayi na tausar zuciya,hannunsa saman kafadar nanay din yana shafawa a hankali kamar me lallashin yaron goye dake rigima. *_BAYAN MINTI TALATIN_* "Nanay" Akhnan ta furta sunan a hankali kamar meyin rada muryarta tana rawa. Kalmar ya fito mata ne ba tare data shirya hakan ba. Idan bata manta ba,cikin diary din safeena wanda bata bude koda third page dinsa ba har yanzu.....amma daga page na farko zuwa na biyu cikin sunaye sahun farko da taga anata maimaita rubutawa akwai KHADEEJA NANAY. a yanzun tana iya tuna haka. "Karki qara kirana da kowanne suna sai wannan" Nanay ta furta hannuwanta cikin na akhnan din tamkar anace mata idan ta saketa zata bace a shafe babin wannan farincikin da yayewar damuwar data samu. Lumshe idanu akhnan tayi,sai wasu hawaye suka biyo ta qasan lumsassun idanunta. Har mutane nawa mamminta ta rasa ne a rayuwarta?,mutane nawa ta tafi tana kewar rashinsu?,da fari ahmad.....ance akwai wani yaron nata daban inji momma.....yanzu kuma ga nanay?. A yanzun ko zata samu salama idan tasan an samu mutum biyu a cikinsu?. (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) Hannu nanay ta sake kaiwa gefan fuskar akhnan tana dauke mata hawayen,ta bude idanunta a hankalin jin hannunta saman Fuskarta,hannun sai ta jishi da wani irin sanyi da wata irin rahama,kwatankwacin yadda takeji akan na morsa safiyya. "Kina da irin idanunta.....kina kallona kamar yadda take kallona" Nanay ta furta da wani murmushi da hawaye ke kwance fal qasan qwayar idanunta. Dauke idanunta tayi ta maida kan haisam,wanda ke tsaye goye da hannuwansa a qirjinsa yana dubansu. Yana ji kamar an kwantar da zuciyarsa ne ana yankar namanta. Kuka na mace baya sonshi sam,ballanta kukan nanay dinsa?. Ya dauka kukan nanay kawai zai masa zafi,amma sai yaji kwantankwacin wannan ciwon sanda yaga gangarowar nata hawayen. "Ina safeenar......Allah yasa tana tare dani" Maganar data sanya komai tsaye musu cak. Wani kewa.....wata qauna ta mahaifiyarta ta taso mata,kawai saita kife kanta sosai saman hannunta dake cikin na nanay qwalla tana zuba. Hakan da tayi ya sanyayar da jikin nanay sosai,cikin mutuwar jiki ta aza hannunta saman kan akhnan tana jin zuciyarta na wani irin bugawa "Ya Allah......ya Allah" Ta fada a hankali,tana neman agaji ya bata juriyar abinda zataji. Gabanta ya zagayo,ya kuma tsugunna saman qafafunsa a nutse. Nutsa hannunsa yayi tsakiyar nata hannun dake cikin na akhnan,sannan cikin softness yace "Allah ya karbi kayarsa shekarun baya da suka wuce,amm....." Daga masa hannu tayi da sauri. "Safiyya fa?" "Tana nan,tana raye,tana agadez cikin qoshin lafiya" Wata iri nannauyan ajiyar zuciya ta sauke,hawaye suna son sake zubo mata amma ta sanya dukka jarumtarta tauhidinta da imaninta da Allah ta danneshi tare da fadin. "Alhamdulillahi ala kulli haall.....Alhamdulillahi sirran wa jahran,Allah na gode maka,daka dauki safeena saika bamu copy dinta.....sannan ka barmin safiyyahta a raye,Allah ka gafarta mata cikin yalwatacciyar rahamarka" Duk da cikin wani yanayi take,amma sai taji amsa addu'ar ya zame mata dole,ta amsa a hankali labbanta suna motsawa. Matso da akhnan tayi zuwa jikinta sosai,wata qauna dukka da takewa safeena tana jin tana tashi tana komawa kan akhnan din. Ta rumgumeta sosai cikin jikinta. "Koda raina ne zan iya bawa safeena.......kisa a ranki safeenanki data mutu gata ta dawo......ni nanay,zan zamemiki sama da uwa idan akwai,duk dana sani.....kin samu komai daga safiyya" Idanunta ta lumshe a hankali,wata nutsuwa tana shigarta,yayin da rayuwarta da momma safiyya ta gilma ta idanunta. "Me ya kawo haka?" Ta tambayi kanta,me yasa haka ya dinga faruwa tsakaninta da momma,me yasa sai daga qarshe take jinta kusa da zuciyarta kaman yadda takejin nanaya a yanzu? "Ya sunanta.....sunanta na gaskiya" "Khadeeja nanay.....sunanki aka mayar" Ya fadi sunan da wani irin yanayin da zai tabbatar maka yasan asalin sunan yadda yake,yadda ya fada ya qarawa sunan dadi da daraja,ya lumshe idanunsa yana budewa akan akhnan wadda tayi suman zaune. "Ya akayi yasan every details haka a kanta?,yaushe yasan sunan Nanay aka saka mata?,da gaske sunan nanay dinne?,wanne irin aminci ne haka a tsakaninsu?,zataso taji......zataso ta samu wannan cikakken labarin. "Allah sarki....Allah sarki" Kawai nanay ke maimaitawa tana tuna girman qaunar dake tsakani. "Nanay.....kun manta damu?"muryar noorah wadda tayi magana a shagwabe da Aanani ta turota ya ratsa kunnnensu. Bata shigo parlor din ba,tana daga bayan qofar tayi maganar. Yanayin maganarta ya bawa haisam da nanay dariya,akhnan batace komai ba,don da harshen oromo tayi magana bata gane me tace ba,bayan siririyar muryar dake nuna mata qaramar yarinya ce take magana. "Zamu qarasa magana nanay" Ya fada yana miqewa a hankali yaja baya. "Tabbas......ya kamata takwarata tasan wace mamanta....kama matarka ta tashi" Nanay ta fada tana zame hannunta daga cikin na akhnan,saidai har yanzu ta gagara daina kallonta,da wani irin murmushin qauna da soyayya shimfide kan fuskar nanay din,saita soma takawa tana nufar qofa ganin akhnan din taqi motsawa,alamu kunya dukka suna bayyana a tattare da ita *zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 08187255862 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 08187255862 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽 💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 61* Idanu sosai ya zuba mata bayan fitar nanay din,a hankali ya tako zuwa gabanta. Da gaske tausayinta yakeji sosai yana ratsa cikin zuciyarsa,irin tausayin da bai taba jin irinsa akan kowa ba. Ya lura akwai wani nauyi na nanay dake tsakiyar qwayar idanunta,to amma baisan meye ya kawoshi ba. Bai tsaya miqa mata hannu ko yin magana da ita akan ta tashi ba. Kawai ya sanya dukka hannuwansa biyu ne ya dagota. Ya dagota ne a bazata,wannan ya kassara kowanne karsashi nata ya sanya ta fada jikinsa hankali kwance. Wannan faffadan qirjin da qamshinsa ya zame mata JARRABI....qamshi na biyu kenan a duk duniya da take jin yana fiddata daga duniyar da take bayan qamshinsa na anihi da wannan turaren da na shuwa incense and more. Hannunta tasa da niyyar tureshi,saboda irin wannan rungumar da yayi mata ya sanya dukka qarfinsa ya riqeta da kyau,don haka ko motsawa kafadunsa basuyi ba ballantana ta saka ran zai matsa daga kusancin da yake tsakaninsu. Batason wannan kallon.....wannan kallon na tsakiyar idanu da yake mata,yana qara yawaita rauninta,yana sake sanyawa ta jita wani iri,yana kuma sake haukata yanayin da takeji cikin jikinta. Sosai yake kallon cikin idanunta,wanda hawaye ya jiqe mata eye lashes dinta ya sake sanyawa suka zama zara zara. Yatsansa ya miqa a hankali ya dora saman eyelashes din,taja wani irin numfashi tana lumshe idanun nata. Hakan sai ya qara mata kyau sosai a idanunsa,hawayen suka zama kamar wata rumfa tsakanin qwayar idanuwan nata. Yatsu uku ya sanya yana goge mata hawayen a hankali yana sake kallon fuskarta. Komai nata na zaune akan tsari.....komai nata kaman ta zaba....komai yayi daidai da yanayinta da sigarta. Cikakkiyar girarta data dace da hancinta me tsaho da tudu.....dan qaramin bakinta me dauke da siraran labba..... A duk sanda yatsunsa suka sauka saman fuskarta sai taji wani abu yana ratsa sassan jikinta,wani abu me kama da yawon kiyashi a jikinta. Can qasan ranta kuma tana sake juya komai a kansa,zuwa yanzu al'amarinsa ya fara bata tsoro.......al'amarinsa ya zarta dukka inda take zato. "Yaushe?,ya akayi?,ya akayi yasan komai daya danganceta?,komai daya shafeta?,harda tsohon tarihin da ba ita kadai ya shafa ba?,mahaifiyarta ya shafa kai tsaye?" "Waye kai?" Ta sake fadi idanunta a lumshe,amma wanna karon cikin wata karyayyiyar murya. A wannan karon cikin wani irin yanayi dake nuna tsananin buqatar son sanin WAYESHI din. Shuru yayi yana qarewa lips dinta kallo,ba magananta ne ya dameshi ba,lips dinta ke burgeshi,burgeshi sukeyi har yana jin jikinsa ya fara amsawa,mararsa ta sake motsawa tana dan daurewa da wani irin yanayi daya tabbatar mode dinsa yana dab da canzawa. Yana jin kamar ya kamo lips din,yayita tsotsa da wannan sulbin da suke dashi wanda tunasu kawai yana iya birkita lissafinsa. "Ka fara bani tsoro" Ta fada tana bude blue eyes dinta a kansa. Yarrrr yaji tsigar jikinsa ta zuba,ta bude idanun nata ne da wani irin yanayi da ya sanya ya kasa jurewa,sai ya sake sakata a jikinsa sanda take yunqurin zamewa,ya mannata sosai da jikinsa yana aza dukka tafukan hannayensa akan mazaunanta. Tudunsu ya cika masa hannu,ya lumshe idonsa yana hadiye yawu da qyar. Saukar hannun a gurin ya sanyata wani irin zabura,ta sake yunquri ta zame hannuwan amma sam bata da wannan qarfin,sai ta maida idanunta kansa. "Please" Ta fada da wata narkakkiyar murya,ga zatonta yanayin zai taimaka mata ya saketa,saidai ba abinda hakan ya haifar sai sake kunnashi da tayi,don kai tsaye ya kwantar da kansa saman kafadarta,take taji yadda yake kokawa da numfashinsa. "Please" Ya sake maimaita kalmar data fada din a rarrabe saboda yadda zuciyarsa ke bugawa. "Na shiga uku" Ta fada can qasan ranta idanunta suna tara ruwan qwalla. Me yasa?,me yasa yakeson mannewa jikinta haka?. "Obbooooooo" Muryar noorah ta cika masa kunne wadda still tana daga bayan qofar ba tare data shigo ba. "Ya salammmm" Ya fada yana janyewa daga jikinta. "Noorah" Ya amsa mata da birkitacciyar muryarsa. "Muna jira obbo please" Ta fada da yaren oromo. "Alright" Ya amsa a kasalance. A nutse ya warware hannayensa daga inda ya dorasu,ya janye baya a hankali yana Ciro tissue ya miqa mata. "Ki goge hawayen fuskarki,ni a yanzun bani da mafita na sani sai a gurin Allah" Hannu ta miqa tana karbar tissue din tana zube idanunta cikin nasa,yaga tambayar dake yawo cikin idanuwan don haka yayi taku biyu sannan ya dora da fadin. "Mamminki na daya daga cikin mutane mafi soyuwa a zuciyar nanay......mun tashi mun sameta cikin kewa qauna da soyayyarta,ta yaya zata bari wani abu ya taba jinin wannan halittar?" Tissue din ta dora saman fuskarta tana goge hawayen da yayi saura a hankali,tana jin wata soyayya da qaunar matar tana saukar mata,tana kuma jin tamkar mahaifiyar data rasa dinne ta dawo kaman yadda ta buqaci taji hakan. "To amma meya banbanta ta.....me ya banbanta wannna yanayin da abinda takeji akan morsa safiyya?,me ya hana taji wannan yanayin da wuri akan morsa safiyya?". "Mammina......kusanci da mammina" Zuciyarta ta bata amsa kai tsaye,amsar data tsaya cak cikin kanta tare da riqo hannunta da haisam din yayi cikin nasa yana fadin. "Muje" Tadan kalleshi kadan,suka hada idanu sai ta basar. Ta fahimci kamar ya soma sabawa kansa da wasu abubuwa game da ita,kaman riqe hannunta,yana nema yayi normalizing din abu gaba daya. Kanta ta daga cike da wani hargitsi sanda nanay ke fitowa,ta dauka zata gansu su ukune,shi nanay din da matar tashi,saidai ganin nanay ita kadai ya sanyata kafe nanay da idanu,maimakon tarin tambayoyin da su noorah suka baibayeta dashi, Murmushi ta sakar musu tana zama tsakiyarsu. "Ba iya surukata kawai haisam ya kawomin ba......harda tsohon mafarkina.....tsohon burina dukka ya tattara ya kawomin,diyata haisam ya shiga duniya ya nemo min.....bazan gaya muku wace ba,zanga waye zai iya gane me nake nufi bayan ta fito" Ta fada tana murmushi. Cecekuce suka fara a tsakaninsu,kowa yana son canka,kowa yana son fadin albarkacin bakinsa,saidai ga saamee kuwa,wani qarin firgicin ta sake shiga, Wacce diya ce ta nanay bayan su dinnan dake gabanta?,wacce diyace haka data samarwa nanay wani irin launin farinciki daga shigarta gurinta wanda ta dade ita bata gani ba a tare da ita?. (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) Kacamewar da sukayi da magana sai ya hadu da tunanin qwaqwalwarta kwanyarta ta soma nauyi,nauyin da bata fahimci me girma bane sai sanda idanunta suka sauka kan farar qafar haisam data fara shigowa wanda ke sa ye cikin lallausan baqin takalmi na fata. A hautsine tayi gaba kadan da idanunnata,suka sauketa kan qafafun akhnan din dake dauke da zara zaran yatsunta da suke da alamun ragowar lalle a rabin kowanne farce. Da wata nutsuwa data tilastawa kanta,da wani matsanancin bugun zuciya take daga idanunta don isa ga fuskar akhnan da take bala'in dokin son ganinta. Wacece ita?,me zata gwada mata?,dame ta fita?. Daidai sanda idanunta suka kai kan fuskartata,daidai sanda akhnan din ke daga kanta a hankali tana laluben fuskar noorah. Ta riqe muryar yarinyar da tayi kiransu har sau biyu a dazu,shi yasa a yanzun data sake jin muryarta dab da ita ta daga kanta don ganinta. Wani sashe ne na zuciyarta taji ya zaftare daga qirjinta yana neman hanyar da zai fado. Wani tsoro shock da wani irin razani ya mamaye ruhinta zuciyarta gangar jikinta dama b'argonta gaba daya. "Ya Allahu.....ya Allahu" Ta fada can qasan zuciyarta bakinta yana rawa,kaman yadda hannuwanta da qafafunta dukka suke rawa. Takawa takeyi a hankali,idanunta har yanzu a qasa kadan,hannuwan noorah cikin nata ta riqesu da kyau cikin siraran yatsunta. Ta dauka zata ganta macace kamar kowacce mace,amma sai take ganin wata TAFISU....wata mace da sunan macen kawai tayi tarayya dashi da sauran mata.....amma komai nata na dabanne. Komai nata yana nuna ainihin ma'anar kalmar KYAU.....yanayinta zubinta gaba daya yana nuna asalin abinda IZZA da qasaita ke nufi. Bata zauna da ita koda na minti.uku ba,amma daga nan inda take zaune abubuwa take hanga tattare da ita masu nauyi. Idanunta yakai kan blue eyes dinnan nata,wani nau'in kalar blue eyes da bata taba ganin irinshi ba. Wata irin fuska da aka azurtata da sassanyan kyan da ko ita ta sani KYAKKYAWA ce,duk yadda takeji a lokacin bata isa ta qaryata wannan ba.....hasalima yana daya daga cikin abu mafi daga hankali da birkitata a yanyanzun Wata irin tafiya take majestically,natural grace,blue eyes dinta ta sake kalla,ba irin wanda ta sani bane,ba kuma irin wanda ta saba gani bane. Wannan kalan blue din me wani irin kyau ne da wani haske me daukan hankali a cikinsa. "Ta yaya zai iya tsallake idanuwansa daga kan wannan halittar?" Wata zuciyar ta rada mata a hankali,saita maida idanunta ta lumshe tana jin haushin gaskiyar da zuciyartata ta gaya mata,tana jin yadda bugun zuciyartata ke sake ninkuwa,yana kuma sake tsananta da wani irin mahaukacin kishi. "Ta fini.....ta fini tako ina na yarda.....amma na fita kusanci dashi,na fita kusanci da nanay,na fita kusanci da sanin komai da yakeso,don haka ina da nawa quality din,ina da sauran quality din da zan karbeshi" Ta fadawa kanta a hautsine tana sake bude idanunta tarwai a kansu. Wannan karon daya hannun nata dake cikin na haisam idanunta suka sauka. Yatsunsa cikin nata ya sarqafesu sosai kaman wanda ke tsoron zata subuce masa. Karo na farko.....lokaci na farko a rayuwarta da taga hannunsa cikin na wata d'iya mace. Wadannan zara zaran yatsun nasa da suka jima suna burgeta,wannan yatsun nasa da takan jima tana kallonsu musamman idan yana rubutu da wani irin salon burgewa dake jan hankalinta. Wani abu ne zafi ya sake matse zuciyarta. "Zo nan d'iyata" Kalmar nanay ta sanya kowa ya koma cikin nutsuwarsa,ta fada ne saboda tayi saving akhnan kan yadda rumaisa Aanani da noorah suka baibayeta kowa yanason ta fara bashi kulawarta. Da idanun nan nata take kallonsu.....wani irin kallo daya motsa asalin farinciki daga zuciyarta. Murmushi ne kwance saman fuskarta ba tare data sani ba,dukkaninsu burgeta sukeyi,burgeta sukeyi da wani irin yanayi da bata taba sanin akwaishi ba. Family guda....ahali guda.....iyali guda,wasu na kama da wasu a cikinsu,nutsuwa da tarin kamewa da qaunar da take gani tasu a idanunta. Me ta musu data cancanci wannan soyayyar da kulawar?. Kama hannunta nanay tayi,ta zaunar da ita saman kujerar data tashi. Idanu saamee ta lumshe nauyin qirjinta yana neman rinjayarta. Wata kalar girmamawa take gani daga gurin mama oromo.....mama oromo me tarin girma da kuma matsayin da ita kanta tasan ba qarami bane. Ita take tashi daga muhalli sannan ta zaunar da wata?,wani babban alama na qarshen girmamawa a al'adarsu. *zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 08187255862 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 08187255862 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 62* "Waye zai iya gayamin.....diyata ta wanne bangarene?....ni kuma na bashi kyautar da bazai manta da ita ba" Ta fada tana murmushi tana kuma rarraba dubanta tsakanin fuskokinsu gaba daya. Murmushin dole saamee ta qirqiro sanda idanun nanay ya sauka akan fuskarta. Ta motsa bakinta kadan,saidai wani abu daya dunqule mata a wuya ya hanata cewa komai. "Ina ganin kamanni nanay,saidai banason fada na daga miki hankali" Balqess ta furta a hankali idanunta akan akhnan wadda kanta yake qasa har yanxu,hannuwan noorah kuma suna cikin nata. Yarinyar taqi yarda sam ta matsa daga kusa da itama,tana jinta a yau a yanzu kamar tana cikin family dinta,kamar tana cikin ahalinta,wani irin sakewa da wani farinciki dake huda zuciyarta. Daga sanda ta biyoshi kawai ta dauka ta rasa komai nata......amma a yanzu da take ganin abubuwa tamkar musanye akayi mata zuwa mataki na gaba. Daga shehnaz da aisa kawai take samun irin wannan abun da sakewar,amma a yanzun saiga ninkinsu a gabanta kowa na qoqarin nuna mata kulawa. "Safeena nanay.....momma safeena idan zan iya tunawa daidai" Balqess ta fadi tana kasa jiran amsar nanay to umarninta na fadin abinda ke zuciyarta. Sunan ya daki zuciyar saamee,ba ita kadai ba,indai zaka zauna da nanay na kwanaki uku saika san da wadannan mutanen guda biyu. Safiyya da safeena,tana jin bugun zuciyarta har cikin kunnenta,ta daga idanunta a hankali tana saukewa kan fuskar akhnan kafin ta janye,kunnuwanta na jiye mata sanda nanay ke bada tabbaci. "Itace.......jinin safeena ce ta dawo,saidai mun rasa safeena.....amma alhamdulillah,safiyya tana raye". Ko na second daya ba zata iya sake zama a gurin ba haka taji,saita motsa qafafunta da takejin kamar sun mace,ko kuma basa iya amfani a jikinta,ta miqe tana sulalewa gami da nufar qofar fita a parlour din. Kawai tana jin tata ta qare......tana bata da wani sauran hope akan wai soyayyar nanay zata buda mata.hanya a zuciyar haisam,don koda wasa ba zata hada soyayyar safeena da tata soyayyar a zuciyarta ba. Yadda kowacce ke sake mamakin abun ya ajiye wani abu me girma game da mutanen a zuciyar akhnan. Sai taji ta matsu ta sake samun cikakken haske.....da cikakken tarihin alaqar mamminta da wadannan ahalin. "Ya akayi yasan da wannan alaqar wai?" Ta fadi tana satar kallonsa ta can qasan idanunta sanda yake tsaye hannayensa goye a qirjinsa,lokacin da aka gama shirya kyautukan mama oromo hajiya khadeeja yunnus jallata a gabanta. Abinda ya sake bata mamaki,yadda kowa a cikin su ya shiga bada umarni ana shigowa da tasa kyautar.....kowa ciki harda auta noorah. Wani abu da taji ya burgeta,wani abu daya alamta mata tabbas akwai qauna da shaquwa me girma a tsakaninsu,tasa hannu ta tallafi akwatin da noorah ta bata na tata kyautar. Ta kasa budeshi tana juyashi kawai a kunyace. "Kyautar maraba daga iyalin motii aba jifar ne wannan" Zenebu ta fadi tana rusunawa a gaban akhnan. "Na gode.....na gode qwarai" Ta fada da harshen turanci wanda kusan dashi suketa magana,don har yanzu ba cikakken communication a tsakaninsu. Kadan kadan take tsintar yaren oromo din,wanda shima bai wuce gaisuwa ba irinsu akkam jirta da sauransu,hakanan suma basu iya French ba hakanan basu iya yaren Tuareg ba,hausarsu da qyar take fita,abinda zai alamta maka basa mu'amala da masu yaren. "Bazan tafi nabar diyata ba......tuntuni na aike masarauta anyi shela,qafata qafarta,wannan rainon.....wannan tarbiyyar nice da kaina zan qarasa dasata" Nanay ta fadi tana kallon agogo wanda yake nuna yammaci na gabatowa. Kadan ya murmusa,yana zare hannuwansa daga aljihun wandonsa,yadan saci kallon akhnan din sannan ya dauke kanshi. "Duk yadda kikace haka za'ayi in sha Allah". Awa daya tak tasa a dauke duk wani abu daya shafi akhnan daga gidan,tasa aka qara motoci aka kuma shirya komai bisa tsari,suka fara gaba,sannan sukayi sallah tare da cin abincin dare,sa'annan suka wuce zuwa aba jifar palace. Duk wannan abun tana qarqashin kulawa da soyayya ta 'yan uwan haisam,kowa kaffa kaffa yake da motsinta da bata wani irin kulawa. Noorah kuwa tana maqale da ita,kamar wannan matsayin na haisam dukka ta tattara ta maidashi ga akhnan din. Labari take mata kala kala,saidai,muryarta qasa qasa sannan cikin nutsuwa. Ko a tafiya motarsu daya da noorah da nanay da akhnan din. Aanani tayita mita zatabi motarsu,amma dole haka ta haqura kaman yadda sauran suka haqura,kowacce ta shiga asalin nata motocin suka harba zuwa masarautar. Wata DUNIYA take hange daga nesa bawai masarauta ba,manyan katangun da sune suke fara marabtar dukkanin mutumin dake tahowa zuwa ga masarautar. Kafin kuma ya iso dab da ita hasken wadansu irin fitilu su cika idanunsa. Fitilun da duk me kallo cikin nazari da fahimta zai gane cewa ba fitilu bane kawai na ado,ba fitilu bane na banza,fitilu ne dake gaya maka cewa ka kusanto wata duniya dake cike da IKO da QASAITA. Wasu irin hasumiyoyi ne dake nuna tsananin qarfin tsaro na soji da dakarun da masarautar ke dashi,suna nesa da juna amma kuma abun mamakin cikin tsari suke. Yadda jerarrun alatun fitilu suka cika hanyar masarautar,hanyar data miqe dodar har zuwa bakin babbar qofar da tafi kama da qofar shiga wata duniyar.....haka dakaru da masu tsaro kowa ke tsaye akan tsari,a muhallinsa cikin uniform launi da dinki iri daya. Fitilu iyakar ganinka da asalinsu na tagulla ne da zinare,wanda aka sarrafasu da wani irin yanayi me daukan hankalin me kallo. Ba don haske kawai ba,don su nuna alatu gado ne ma masarautar aba jifar......don su nuna girman arziqin da qabilar oromo dukka ke taqama dashi.....sannan su nuna girma da daukakar masarautar ibraheem aba jifar. Da wani irin tsari motocin suka jera kansu,suka kuma fara shiga ta babbar qofar,jerawar bawai don gudun matsewa ba....aah,hasalima sama da mota ashirin na iya shiga ta qofar idan an budeta a lokaci guda. Jerawar na nuna irin tarbiyyar ta tsaro da suka samu wanda ba tsoro sam a cikinta. Daka kalli qofar zakasan itama mix ne na zinare da lu'u lu'u da aka yafasu jikin sassaqaqqen dutsen da yake wani irin qyalli,a jikin qofar zane ne na sarauta dawakai da kuma rubuce na nasarorin masarautar da yaruka har guda uku,hakan sai ya sake zama wani ado me daukan hankali matuqa da gaske. Masu tsaron cikin gidan sun banbanta dana farko da suka tarar. Wadannan tufafin jikinsu silk ne,suna tsaye cikin tsari da wata cikakkiyar nutsuwa kamar masu tsaron wani rufaffen sirri,su suka sanya hannu suka bude qofar gaba daya da sassarfa bayan da suka fahimci sheikh muhammad haisam aba jifar da mama oromo ne ke shigowa masarautar da kansu. "Barka da dawowa ya me daraja" Abinda ta iya fahimta suna fada kenan a duk sanda motor haisam dake bayansu zata gifta daya daga cikinsu,cikin wani kalan rusunawa da girmamawa. Idanu ta janye zuciya da hankalinta gaba daya a jagule,wani tashin hankali yana sauko mata. Abinda take gani a yanzu ya girmi hankalinta,abinda take gani a yanzu yafi gaban tsoro shakka ko kokwanto,yafi mata kama da ALMARA irin wadda hankali bai taba kawowa ba. "Wacce irin masarauta ce wannan?" Ta tambayi kanta tana jin dukka wani qoqarinta yana zagwanyewa. Ta gama sallamawa,wannan mutumin,ta gama miqa wuya wannan shiekh din ba shine sheikh din da suka taso dashi daga agadez ba. Kwanyarta ta gaji da tambaya da tuhuma,ta gama saddaqarwa ba zata taba sanin wayeshi ba sai sanda yaga daman gaya mata da kansa,ko Allah yasa taji. (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) "Amma wanne girman matsayi yake dashi a nan din?,wacce irin masarauta ce me girman iko haka?" Ta fadi daidai sanda motocin suke sake kutsa kai cikin gidan,tana kuma ci gaba da ganin abubuwan almara.....yadda alatu yake magana da kansa......yadda MULKI DA IKO suke aiki ba tare da anyi magana ko an bada umarni ba. "Kin shirya muna iya fita?" Nanay ta fadi a nutse,kalmar data jawo hankalinta daga duniyar tunanin data tafi. Kanta a qasa,jikinta a mugun sanyaye ta gyadawa nanay kai,kaman ana jiran hakanne aka buda mata murfin motar,sannan aka buda ta bangaren nanay din. "Barka da shigowa masarautar oromo.....barka da shigowa ahalin oromia.....jini mafi girma da daraja jinin aba jifar" Wata mata data zube a gabanta kaman yadda sauran matan suka zube ta fadi kanta a qasa sai kace bishiyar da aka dasata bata da niyyar motsawa. "Muna farinciki da kasancewarki macen da yarimanmu me jiran gado ya mallaka.....muna alfahari da wannan d'iyar sarkin agadez". Wani irin tsalle zuciyarta tayi cikin qirjinta sannan ta samu guri ta dire. Maganan matar ta qarshe tana maimaita kanta cikin kunnuwanta, "Matar yarima me jiran gado?,wanne yariman?,an sauya mata wani da haisam ne?,ko kuwa shi dinne?,idan shi dinne ta yaya hakan zai buya a gareta tsahon zamansu?,tsahon wannan lokaci?,tsahon kasancewarta da 'yan uwansa?. " Yau masarauta zata kwana cikin farinciki mara misaltuwa,zukatanmu cike suke da fatan alkhairi a gareku,tare da fatan samun zuriya me albarka tsakaninki da yarimanmu.....yarima sheikh muhammad haisam,jinin oromiyawa" Matar dake duqe har yanzu a gaban akhnan ta fadi,sannan ta yaye wani farantin silver da yafi kama da farantin azurfa Komai da yake kan farantin na zinare ne,sai abu guda daya da haskensa ya dara na komai da yake kai. Qafar akhnan daya ta riqe a hankali ta dora saman cinyarta,a yadda take tsugunnen,ta saka hannu ta ciro wata sarqar qafa me bala'in qyalli da daukan idanu,ta bude marufin sarqar,ta soma sakata a tsintsiyar qafar akhnan din. Wani irin numfashi me tauri samee dake can gefe ta shaqa ta kuma furzar. Wannan sarqar me daraja ce,tsananin daraja kuwa a fadin tarihin qabilar oromo,ba kowanne gida bane.....ba kowacce masarauta bace,ba kuma kowacce suruka bace ake iya mallaka mata ita. LU'U LU'U ne wato zallar diamond,ta dade tana bincike akan tarihinta da asalinta,kasancewarta mutum me yawan bincike akan abinda ya shige mata duhu. Darajar sarqa tana ganin tafi gaban a mallakawa akhnan din ita,amma saidai kuma,ana azata saman qafartata kyanta da darajarta ya sake fitowa,tamkar don saboda akhnan din kawai aka qerata. "Kina cikinmu yanzu,cikin qauna da aminci" Ta fada matar da harshen girmamawa. Miqewa matar tayi da farantin azurfar a hannunta,saidai bata iya tsaiwa gaba daya a gaban akhnan din ba,wata irin tsaiwa ce ta nuna girmamawa. Ta bude wani turare,ta zuba a wani qaramin abu tana miqawa akhnan din. Ta fahimci me take nufi,don haka ta bata dukka tafukan hannayenta ta zuba mata shi. Tun batakaishi jikinta ba ta gane turaren,da sauri ta maida dubanta ga kwalbar. Turaren nan ne dai.....turaren da ya riga ya zame mata jarrabi....turaren nan da tayi nemansa harta gaji.....turaren data dinga nema kamar tayi hauka?,ya akayi suka sameshi?. A sannan ji take kaman ta miqa hannu ta daukeshi,a sannan tanajin ko nawa zata iya bayarwa a batashi. "Mun tsarkake miki guri,mun karbeki da hannu bibbiyu tamkar dama daga cikinmu kika fito" Ta sake fada da murmushi akan fuskarta. Maganar ta sake dokawa cikin kunnuwan saamee,maganganun matar kamar gugar zana sukeyi mata,maganganunta kamar suna fadin cewa.....akhnan ta cinye gurin.....ba zasu sake karbar wata matar daban bayan ita wa sheikh haisam din ba. Wani qaramin kofin azurfa ta sake dagawa ta miqawa akhnan din wanda yake dauke da sassanyan ruwan zamzam,hannunta ta miqa ta karba,amma saita gaza sha. "Sha diyata.....addu'o'in tsari ne daga dukkan abunqi da mugun ido" Nanay tace da akhnan qasa qasa,saidai duk yadda tayi qasa da muryarta hakan bai hana saamee jin abinda nanay din ta fada ba. A nutse idanunta suka fada kanshi,yana tsaye nesa kadan dasu,nesa kadan din da take jin ita kadai take iya ganinsa. *zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 08187255862 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 08187255862 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 63* Kamar an sauyashi daga bakin qofar gidan zuwa shigowarsu ta yanzun da tsaiwarsu. Wani mutum daban take sake gani.....cikin suturar oromo data maidashi wani kamilin matashi. Zaki take gani wanda qananun namun daji sukewa hidima,don ko a yanzun tana hangen yadda hadimansa ke gyara masa zaman rigarsa cikin tsananin kulawa da girmamawa Fuskarsa a tsuke,da wani irin qarancin fara'a daya sanya gabanta tsananta faduwa,qarancin fara'ar kuma daya qara adadin yawan kwarjinin dake shimfise akan fuskartasa. Sannan ya sake kawo wani kwantaccen kyau ya zube a fuskarsa gaba daya. Kaman an ninka kyansa....kamar an ninka kwarjininsa.......hakanan kamar an ninka haiba da kamalarsa. "Yarimanmu me jiran gado" Kalmar ta sake dawo mata cikin kunnenta,saita sake aza idanunta a hankali akan fuskarsa. Tantama take......komai nasa ya sake canzawa daga taku daya tak da tayi zuwa cikin gidan?,komai yanayinsa ya sauya?,anya shine?,shine kuwa?. Firgigit tayi saboda magana da yayi mata,bada bakinsa ba don ko motsawa wani sashe na jikinsa baiyi ba. Da idanu da kuma girarsa kawai,kaman yana cewa. "Kisha abinda suka baki,mutane ne kewaye dake suna jiranki" Sai ta sauke idanunta da suka raunana sosai,suna jinta ta koma wata maqasqanciya,ba kuma don an tozartata ba ko an durqusar da matsayinta ba,aah......sabda cin karo da tata izzar da tayi da IKO da yafi nata tsananin qarfi. Tayi bismillah ta kurba,ta daga kanta a hankali sanda take ajiye cup din saman tray din tana maida idanunta inda yake dazun,saidai a yanzun bata da damar ganinsa.....a yanzu baibaye yake da dogaransa ma'abota fararen kaya,zagayeshin kuma da sukayi ya hana mata daman koda ganin wadannan idanun nasa masu qyalli. Wani bracelet ta miqa mata,na azurfa wanda akayi dukkanin adon jikinsa da qananun duwatsun lu'u lu'u. "Wannan girmamawa ce daga yarima muhammad haisam....." Ta fadi tana miqata ga akhnan. Sake kallon gurin tayi,still bata iya ganinsa,tasa hannu ta karba bracelet din daketa sheqi yana daukan mata idanu,sai jakadiyar ta janye farantin baya,sannan ta soma komawa da baya da baya ba tare data juya ba. Ta fahimci al'adarsu ce haka,sanda duk zasubar gaban me iko basa juya masa baya,saidai suyi qasa da kansu,su kuma janye da baya da baya har su bacewa ganinsa. Wanne irin iko ne wannan.....wannan hanya ce ta shiga cikin iyali ba tare da kalma ba?. Tambayar datawa kanta kenan wadda ba wanda zata iya yiwa bare ya amsata,hasalima miqaqqiyar hanya suka fara bi ita da nanay,jama'ar dake tare dasu suna rarraguwa da kadan da kadan,har suka bulla wani kyakkyawan guri. Shi ba parlor ba.....shi ba hanya ba,amma yana da wani irin girma da aka cikashi da alatun da ya sake sanyayar da jikinta. Komai da ake adanashi a boyeshi domin ado me tsada da daraja......su dashi suke amfani suke shimfidewa a bango da inda qafafu zasu taka?. "Zan tsaya a nan.....muhammad da kansa zai miki jagora,ki kwanta ki huta sosai,zuwa gobe in sha Allah,zamu tattauna sosai,Allah yayi miki albarka diyata" "Ameen na gode" Ta fada tana matse abun hannun cikin tsakiyar tafukan hannayenta. Batasan wanne kalar tunani zatayi ba sam,batasan ma wanne yanayi zatace tana ciki ba?. Nanay ta janye a hankali,idanun akhnan a kanta har tabi ta wata qofa,ta dauke idon a hankali tana dawo dasu inda take tsaye,sai kuwa suka sauka kai tsaye a kanshi. Yana daga gefanta,amma ba ita yake kalla ba. Dab da ita yake a yanzun,sai kuma yanzu ta gane ashe kallon data masa daga nesa maqaryacin kallo.ne. mamaki yana sake mamayarta......yaushe ya sauya sutura?. Shigar dake jikinsa a yanzun tasha banban da wadda suka taho da ita daga palace learning residence. Wata shiga ce ta qasaita a jikinsa a yanzu.....wata shigar girma data fidda kamanninsa sak.....ya koma YARIMA CIKAKKE da wata suffa da bata taba ganinta ba.....da wata kamala ta cikakkiyar SARAUTA da bata taba ganinta ba sai yau cikakkiya a tattare dashi. Idanunsa ya sauke a kanta,sai taji kamar zata narke,sai taji.kwarjininsa ya ninka na baya......sai ta gaza musawa ko cewa komai sanda ya miqa mata hannunsa. Nata hannun ta bashi,tamkar kurame sukaci gaba da takwa suna dosar wata hanya. Duk inda zata sanya idanunta sai taga wani abu daban take takawa,ba tiles bane,ba marbles bane irin na masarautarsu.....ba slate bane.....ba terrazzo bane. Sai da tayi tafiya me tsaho sannan ta fahimci wani irin lafiyayyen granite floor ne me tsananin sheqi sulbi da daukan hankali,wanda da alama duwatsun da aka sarrafashi dashi na musamman ne kuma na dabanne. Wata duniyar take gani a matsayin dakin,duniyar da idan ta daga kanta saman roofing na dakin sai taga cike yake da wasu qananu qananun taurari fal dake bada haske. Tsoro ya kamata taji,ta kuma ji din,saidai data tuna itama daga inda ta fito sai izzarta ta ceceta. Sakinta yayi ya koma baya yana zube hannayensa cikin aljihun wandonsa. Idonsa.ya wani narke yana mata wani kallo da take hangen wasu abubuwa masu tarin yawa cikin idanun nasa,amma ba zata iya ci gaba da kallonsa ba,don narkar da ita yakeyi,saita sadda kanta qasa tana wasa da wannan bracelet din na azurfa da aka bata. "Irinsa ne a hannunki.....na mammi safeena.....yadda aka baki wannan a ranarki ta farko cikin ahalin mijinki haka aka bata......amma mugunta da zallar rashin imani ta sanya mam......" Kasa qarasawa yayi,sai yayi shuru yana hadiyar wani abu. Har yanzu idan ya tuna matar shi kadai yasan yadda yakeji ana yankar zuciyarsa a kanta. Banda akwai wani plan akwai wani wa'adi a kanta ba abinda zai hanashi qarasa hukuntata. Sai daya gama qare mata kallo me isarsa,yana lumshe idanunsa a hankali yana jin yadda mararsa ke dake damqewa Ya sani.....idan ya fita a wannan dakin dawowarsa zai zama wani abu me wahala. Wataqila nanay ta killaceta da tsaro sosai.....wataqila ta hanashi ganinta.....wataqila ta hanashi zuwa kusa da ita.....duk da bai sani ba....zai iya jurewa?,don haka ya fara takawa a hankali,dogayen yatsunsa suna nutsewa cikin lallausan carpet din,suna hana sautin takunsa fita. Batasan ya iso gareta ba,sai da taji an riqe qugunta sosai,idanunta ta daga a nutse tana saukewa cikin nasa. Haka kawai takejin matsayinta gaba daya ya zabtare ya fadi a qasa.....cikin mintunan da basu rufa awanni ba wani sashe can dake cikin zuciyarta taji yana gaya mata. "Wutsiyar raqumi tayi nesa da qasa" Kamar a yanzun da yake tsaye dab da ita,qamshinsa na alfarma daya hade da qamshin da dakin ke bayarwa ya daki zuciyarta sosai,ta farajin kamar da gaske ne,kamar ya tsere matan,kamar akwai wata tazara me girma a tsananinsu. Numfashinta ya tsaya cak sanda taji tattausan labbansa masu sulbin nan saman dokin wuyanta. Wani abu ya fusgeshi sosai da kalar qamshin dake fata daga cikin rigarta. Ya damqe qugunta sosai jikinsa yana shaking,wani irin numfashi me nauyi yana sauka saman wuyan nata. Me yake faruwa ne dashi haka?,me yasa take fusgar hankalinsa haka?,meye dalilin da duk sanda zasu kebe shi da ita yakejin yana da burin rab'ar jikinta?. Me yasa jikinta gaba daya yake burgeshi?,me yasa yakejin wani gushewar nutsuwa a duk sanda ya kusanceta?. (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) Janye jikinsa yayi a hankali yana jan hanci kamar wanda yake mura,ya daga idanunsa a hankali ya sauke a kanta. "Are you okay?" Ya tambayeta da faransanci. Ya saba yadda take matse masa jikinta.....ya saba da gardamarta.....da yadda take nuna lallai bataso ya tabata,duk da wasu sassa na jikinsa sun qaryatata,sun gaya masa qarya yakeyi. Blue eyes dinta ta daga tana dubansa,zuciyarta a yau din a mugun karye take. Donme zai rufeta?,don me zai dade yana yaudararta ita da sultane?,don me zai rufe shi waye?,ma yake nufi?,meye manufarsa a kansu?. Ta tabbata tayi imanin duk wanda zai aikata haka akwai wata manufarsa daban a qasan zuciyarsa,kawai saita kasa controlling kanta da kanta,ta fashe da kuka mara sauti. "Ya salam.....ya Allah" Ya fada da wata kasalalliyar muryarsa yana takowa inda take tsaye,saidai dab da zai iso taja baya tana dubansa. "Me yasa?.....me yasa kayi haka?,me yasa ka rufe waye kai?" Idonsa ya maida ya lumshe na wasu mintuna,yana jin yadda fushi yake tasiri cikin muryarta,sai kuma ya budesu dukka a kanta, "Ban rufe ba....kaman yadda ban bayyana ba,ba zaki fahimci komai ba.....ba kuma zaki fahimceni ba ko a yanxun ma......" Ya fada yana soma takawa da baya da baya ba tare daya juya mata baya ba kamar yadda hadiman masarautar ke mata "ki kwanta......kiyi bacci......ki huta sosai......don Allah" Ya qarashe kalmarsa ta qarshe da wani irin sanyi da taushi sosai kaman wanda keson rada mata maganar sannan ya sake taku uku yana ficewa,saidai har ya fice din idanunsa suna zube a kanta. Fushi takeji nasa a ranta,amma sanda yake fita din sai takejin kamar tace masa TSAYA karka fita....kamar tace ya zauna suyita fada.....ya zauna tayita fada masa abinda yake ranta.....ya zauna ta kalleshi da kyau cikin shigar sarauta. Samun kanta tayi da zama dirshan gefan gado tana hawaye,sai kawai ta sanya tafukan hannayenta biyu saman fuskarta. Ba zatace ga dalilin kukanta ba......amma haka kawai tana jin zuciyarta a wani matuqar karye. *_AGADEZ PALACE_* Cikin dukkanin tsari da umarni yake tafi da motsin komai na masarautar. Ya yadda ya kuma amince d'ari bisa dari mulki ba abu bane na wasa.....wani babban aikine daya sanya a kwanakin ya sake sarawa sultane. Ba wasu matsaloli bane masu yawa,amma aikin kulawa da masarautar ya zame masa na dabanne saboda ZAITUNA. Akwai tarin tsare tsare da dokoki da aka sanya wajen shiga sassan sultane gaba daya. Kowa da kowa....don dokokin sun shafi harda matansa. Tun daga abincinsa.....maganinsa dama komai daya shafi lafiyarsa ta hannun ahmad kawai aka yarda ya fito,zai kuma katse komai da yake a duk lokutan wadannan ayyukan duk da hidimar tafiyar da masarauta yaje yayi masa sannan ya koma bakin aikinsa. Kamar yanzu a wannan daren da suka kammala zama da tattunawa da manyan members na fada. Sha daya ne na dare,kuma lokacine da yawancinsa sultane bacci yakeyi,baya kuma farkawa sai dab da sallar asuba. Wani iko na Allah,baya taba gota lokacin salloli komai tafiyar da yayi,lokaci yanayi zai farka,a taimaka masa yayi sallolinsa ya koma. Shima a wannan lokacin yake zuwa sassansa yadan runtsa,zuwa cikin dare ya dawo gareshi har zuwa asuba. Sassan nasa sunyi shuru,sai amintattun masu tsaro da aka cika bangaren dasu. Ba kasafai ya fiya karbar gaisuwarsu ba a irin wannan lokacin,don ba lokaci bane na gaisuwa,lokaci ne kawai.na kulawa da motsi da lafiyar sultane,a haka har ya isa ciki. Daya bayan daya yake buda qofofin,an killace ko ina an rufe da tsaro,don ba lokaci bane na shigowar kowa,lokaci ne kawai da yake kwanciya bacci sai kuma asuba. Idanunsa ya kafe daya daga cikin dakunan baccin sultane,wanda ya saka aka maidashi dazu da safe saboda ya samu canjin muhalli. Qofar yake gani kamar an budeta,kamar bata rufu sosai ba,wannan abun ya sanyashi qara hanzarinsa cikin salo na sand'a da kuma sassarfa,saidai dab da zai isa gurin qofar ta bude,gangar jikinta ya fara fitowa sannan kanta wanda ta juya tana waiwayen cikin dakin. Dawo da ganinta da tayi gabanta ya sanya suka hada idanu da ahmad,yana tsaye qyam ya zuba mata wadannan rinannun idanun nata da tun yana dan qwaya suke mata wani iri. A hankali ya sauke idanunsa kan gorar ruwan C'bone dake hannunta,sai itama tabi robar da kallo,sannan idanunsu suka hade guri daya lokaci guda. *_Tooooo......su zaituna dai ba za'a canza hali ba......da alama tana wasa da wannan talalar me kama da SAKE_* *_Muje zuwa....akwai kallo fa jama'a_* *_Saamee dai ta rantse.....taci alwashi......A INA NASARAR TAKE NE?_* *_Me MAMMINA TA SHIGA YI DAKIN SULTANE?,...._* *_WAISHIN wanne irin plan ne da SHEIKH MUHAMMAD HAISAM ABA JIFAR AKA AL_SAAMIT(THE SILENCE ONE)_* *_ME YAKE DAMUN SULTANE NE?_* _KU MAQALQALE HUGUMA😂😂,ITA KE DA AMSOSHIN TAMBAYOYINKU IN SHA ALLAH_ *zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 08187255862 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 08187255862 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 64* Wani irin kallon kallo suke yiwa junansu shi da ita,wani irin zuzzurfan kallo dake nuni da zallar abinda ke cikin zukata sukewa junansu. Kowa kawai qoqarin mallakar kansa yakeyi,musamman ahmad daya samu wani irin training daga gurin haisam na dan zaman da sukayi tare. Kallon dake cikin idanun ahmad din sun mata nauyi,saidai ko daya taqi yarda ta bari yaga haka cikin idanuwanta. Ya motsa zuwa gaba kadan,cikin wata kakkaifar murya yace. "Bansan me kikeyi a nan a daidai wannan lokacin ba" Idanu ta sake zuba masa,sannan ta saki wani shu'umin murmushi tana gyara tsaiwarta. "Yaro man kaza......" Ta furta da wani yanayi,sannan ta mamaye maganar tata da fadin. "A daidai wannan lokacin,yanayin lafiyarsa yana iya sauyawa.....kai bakaga kamata gurin zuwa dubashi akai akai ba?". Idanunsa ya qanqance sosai a kanta. " Anyi masa komai daya kamata....baya buqatar wata qarin kulawa ta daban tunda ba lokacin tashinsa bane.....bayan duka wannan kin sani......doka ce an hana kowa shigowa gurinsa irin haka" "Kowa?....kowa?" Ta maimaita sau biyu tana kallon ahmad din. Can qasan ranta tana jin wani b'acin rai yana ratsata. Wai sai yaushe komai zai saitu?,yaushe lalacewarta yakai haka?. Yaron data raineshi da hannayenta,yaron data bashi rayuwa irin wadda takeso,yaron daya zama tamkar bawa a gareta yau shike da iko da fada a ji cikin rayuwarta data masarauta gaba daya?. Ba shakka da tasan zai zama haka.....zai mulketa koda na rana d'aya ne tabbas data kasheshi bata bari taga zuwan wannan ranar ba. "Ni ba kowa bace.....bana cikin sahun jam'in KOWA da doka zata hau kansa" Tayi maganan a hanzarce tana takowa don wuceshi. Alwai wani abu dangane da yaron,akwai wani abu da bata so da yake qyalli cikin idanunsa,kamar shige shigen abinda yake fita daga idanun sheikh haisam. Da kallo ya bita,yadda ta fita din baiyi masa ba,a gaggauce da yanayin da yake gaya masa lallai akwai wani abu da take birnewa,sai kawai ya ciro wayarsa,yayi kira dukkanin qofofin da zata fice,ya bada umarni tsare masa ita har sai ya tabbatar da komai na sultane lafiya yake. Wayar ya ajiye,sannan ya fara takawa a hanzarce yana wucewa dakin sultane din. Ya daga labulen yana shiga bakinsa dauke da sallama,duk da ya sani babu me amsa masa. Ba kowa kaman yadda ya zata,yaci gaba da takawa zuwa inda yake. Yana nan kwance kaman yadda ya barshi,ba wani abu daya canza daga fuskarsa ko yanayin kwanciyarsa. Yakai hancinsa zuwa bakinsa da hancinsa ya tabbatar da bugawar zuciyarsa yadda take. Wayarsa ya ciro kai tsaye,ya kuma kira haisam,daidai sanda yake tsane kansa da towel bayan ya fito daga wanka da ruwa me dumin gaske saboda yadda mararsa har yanzu taqi sassauta masa. Shuru yayi yana sauraren dukkanin bayanan ahmad,har sai da ahmad din ya kammala. Ka bincika dakin,komai da komai,qasan shimfidarsa,gefe da gefan gadon,kada ka sanya hannunka,kayi amfani da hand glove,bayan labulaye,cikin pillow dinsa,toilets da bathroom" Abinda yace dashi kenan. "Ka maida kiran video call,ka ajiye ta inda zan iya ganin motsinka" "Yes sir" Ahmad ya amsa masa da girmamawa. Miqewa haisam din yayi,yana gyara daurin bathrobe din jikinsa sosai,sannan ya koma ya zauna yana amsa video call din da Ahmad yayi requesting masa. Ya sani,ba yadda za'ayi tayi shiga da fitar banza. Duk sanda ka ganta akan abun hari to lallai ba shakka akwai wani saqo da zata bayar ko ta aiko a bayar din. A nutse yake monitoring motsin ahamd,yana bincike ko ina idanunsa suna biye dashi har ya kammala,saidai ba wani abu da aka samu. "Ka kuncemin Ac dincan" Haisam ya fada a nutse yana duban ahmad. "Kafin ka kunce,ka samu bargo ko wani abu me laushi ka shimfida daga qasan,incase ko meye karmuyi losing nasa" "Tom" Ahmad ya fadi,kujera da duk abinda za'a nema haisam ya lissafo masa,Ahmad din ya cire babbar rigar jikinsa yabar 'yar ciki,ya taka kujerar yana bin abinda haisam yace masa step bai st Cikin mintuna biyar ya kwanceta. "Ka ajiye screw driver din,kasa hannunka duka biyun ka tallafe fuskar" Yace masa. Hakan yayi,ya kuma sauke fuskar Ac din a hankali,sai ga wasu qananun kwalabe mitsi mitsi an huhhuda tsakiyarsu kusan guda biyar. Gaban camera din ahamd yazo ya jera masa su yana huci,zuciyarsa tana wani irin tafasa gumi yana tsatsafo masa a goshinsa. "Me muke jira da matar nan obbo?" Ya fada a ladabce,saidai hakan bai hana bayyanuwar fushinsa ba. Wani murmushi ya saki,siririn malalacin murmushi sannan ya maida idanunsa ga ahmad. "Sultane ahmad......sultane kadai muke jira" Ya amsa masa idanunsa cikin na ahmad din. *_A B A J I F A R P A L A C E_* Babban dakin taro ne me cike da wani irin alatu na alfarma.......lafiyayyun kujeru farare da table table masu daukan hankali da nuna alfarma. Chandelier masu na asalin dutsen crystal masu tsananin tsada,masu tsaho ne sosai sun mamaye roofing dakin taron da wani irin yanayi da zai sake nuna maka zallar alfarma da IKO dake tattare da gurin gaba daya. Rana ce data kasance ta farko cikin tsarin karbar baquwar dake aure da jinin aba jifar. Saidai al'adar ta kasance ta daban data dauki hankulan duk wani me iko da duk wanda ke rayuwa cikin masarautar. Sati biyu......sati biyu tayi hannun nanay suna wani irin karatu wanda daga ita sai nanay din. Sati biyu nanay tayi tana bata kulawa da kanta,sati gudan da koda su Anaani nanay bata bari sun ganta ba sai da qyar,ballantana haisam da saidai wani lokaci taji muryarsa kawai. Wani irin shaquwa.....qauna da fahimtar juna masu tarin yawa ne suka gilma tsakanin nanay da Akhnan din. Da gaske,har cikin jininta takejin nanay din kamar safeena......kamar mahaifiyar data rasa din. Ko nanay bata fito kai tsaye ta gaya mata ba,ita din ta fahimci wata gagarumar soyayya da nanay kewa haisam. Jiya ta fara b'aro mata wani karatu data dinga jin kamar zata nutse. "Dokoki da qa'idar daya kamata kowacce mace ta kiyaye......mu'amalar auratayyarta da miji......yadda zaki kai kanki ga mijinki,yadda zaki karbeshi a duk sanda ya kawo kansa gareki......yadda zaki karanci yana cikin buqatarki........da yadda zaki bashi kulawa" Duka sanda nanay ta jero kasa hada idanu tayi da ita. Sarai nanay taga hakan a tattare da ita,amma tayi kunnen uwar shegu kaman bata fahimci Akhnan najin nauyi ba. Abu daya kawai dakewa nanay dadi shine......wata irin kwanya data fahimci Akhnan nata ita.....saurin ganewa da dauke komai,har wani lokaci murmushi yakan kubce mata,can qasan ranta kuma takance. "Bansan wadanne irin yara zaku haifa ba keda Muhammad......kamar sai daya gwada ya samu mace me shige basirarsa?". Cikin wata shiga ta alfarma ta fararen tufafi Akhnan din ke zaune,fararen tufafin da fararen duwatsun dake jiki suka qara musu wani irin kwarjini da daukan hankali. (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) A iya kwanakin al'amuran sun sake sanyayar mata da jiki. Tana ganin wata sabuwar duniya.....sabuwar rayuwa.....sabuwar daular masarautar da kamar za'a ciyar da kai da lu'u lu'u. Karo na farko data fara sanin cewa SAMAN KOWANNE MULKI AKWAI WANI.....SAMAN KOWANNE IKO AKWAI WANI......SAMAN KOWACCE IYAWA AKWAI WATA.......SAMAN KOWACCE ALFARMA AKWAI WATA. A iya suturun da aka ware mata kawai ta sani sunkai adadin abinda ta mallaka a rayuwarta......tabbas inda narka kudinsu za'ayi ba abinda zai hana sukai adadin dukiyar da take taqamar ta mallaka. Kullum idan ta kwanta zuciyarta na cika da mamakin ME YAJE YI AGADEZ?.....me yasa ya qasqantar da kanshi?,me yasa ya zabi wofantar da dukkan wannan gatan nasa da yake dashi?,ya zabi rayuwa qarqashin alfarma?,bayan alfarmar shi take bi da kanta?. A kwanakin idan tace zuciyarta daidai take tayi qarya. Ta samu dukkan kulawa da walwala,wani irin jiqaqqen gata.....amma aduk sa'ilin da dare zaiyi sai wata irin kewa ta taso ta danneta. Sai wata irin kewa ta rugo ta lullubeta......wata irin kewa da sannu a hankali ta fara sallamawa ta fara tashi daga SABO ta fara juyewa zuwa wani abu na daban......wannna abun da har yau bata yarda da kalmar SOYAYYA bace. Dukkanin wasu qawaye.....matan sarakuna......dama matan dake da iko da fada aji cikin masarautar aba jifar ne tattare a dakin. Murmushin dake fita daga fuskar mama oromo kawai zai gaya maka rana ce ta musamman. Daga daya bangaren tana zaune ne cikin rukunin kujerun da iyali kuma jinin nanay da abba jifar ke da ikon zama. Saamee ce,da dukkanin idanunta da motsinta yake kan Akhnan,ba'a iya yau kawai ba......a dukka kwanaki goma sha hudun bata yarda koda kwana daya ya kufce mata ba tare data kusanta kanta da ita ba,ta kuma bar mata shaida da tabon da zata gane ITACE SAAMEE ba. A kwanaki sha hudun,tayi dukka qoqarinta na neman kusanta kanta da dukka hidimar data shafi sheikh muhammad haisam din,a sanda al'ada ta nesantashi da Akhnan din. Kwanakin sun mata dadi,sun kuma maido abinda take kalla da sunan kulawa tsakaninta da haisam din. Saidai a yau dukka farincikinta yana neman rushewa,muddin wannan taron ya gudana yadda al'ada tace.....to Akhnan ta taka mataki na farko mafi girma da qarfin da zai tabbatar da sunanta cikin na haisam dama na masarautar.....zata koma amsa sunan KHADEEJA MUHAMMAD HAISAM JIFAR maimakon KHADEEJA MUHAMMAD HAMMUD. Amsa wannan sunan kuwa shi yake nufin nan da kowanne lokaci zata tare a gidan da zata zamto sarauniya mafi girman iko,gidan da jaridu suketa maganarshi,ya shiga bakin 'yan media da al'ummar gari saboda baqon tsarin ginin da aka masa da tarihi bai taba zuwa da wani wanda ya mallaki irinsa cikin Ethiopia da kewayenta ba. "Takwarata ce......wadda ta fito daga tsatson mutum mafi soyuwa a gareni.......saidai daga yau tabar amsa sunan Akhnan......." Muryar nanay tayi amsa kuwwa cikin dakin taron daya dauki wani irin shuru kamar babu me rai a cikinsa. "Tun daga yau.....tun daga yanzu ba baquwa bace......" Ta sake fadi a nutse,sautinta yana ratsa shurun. Sai ta miqe sannu a hankali da wannan haibar nutsuwar da tarin kamala. Gaban Akhnan ta qarasa,ta miqa hannunta ta riqe hannun Akhnan din sosai cikin nata,sannan tadan dagashi sama kadan "Za'a kiraki......." Ta sake dakatawa tana numfasawa da wani irin zaquwa tarin qauna da soyayya "GIIFTII(giiftii a yaren oromo yana nufin mace me daraja ,macen data fito daga gidan sarauta iko ko matsayi,ko macen da ake girmamawa sosai)" *zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 08187255862 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 08187255862 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 65* "Giiftii" Sunan ya maimaitu cikin kan saamee tare da muryoyin da suka maimaita sunan a tare. Tasan kuwa abinda ta fadi yanzu hakan nanay din?. Sunan giiftii?,ta yaya zata dauki suna me daraja irin wannan ta bawa macen da bata fito daga asalin qabila da yarensu ba?. Ta yaya zata bari haka ta faru?. Qasa Akhnan tayi da kanta,tana jin wani nauyi hawaye suna taruwa a idanunta. Me yasa ya zabi daukota ya kawota cikin wannan tarin girmamawar?,bayan ba wani babban abu da tayi masa data cancanci haka?. Meyasa ya tsallake kowacce mace sai ita?,meyasa ita ya zaba?. Wannan kalar halittan bai cancanci SO ba kuwa?.....me zaki sadaukar masa da zaiyi daidai da karamcin daya shimfidawa rayuwarki?" Tuhumar da zuciyarta keyi mata kenan. Wani irin girmansa taji yana hauhawa cikin ranta. Wannan sunan shekaran jiya cikin bincikenta akan qabilar ta gano girma da matsayin sunan.....ta gano irin masu girman matsayin da suke ake bawa shi.....yaushe ta cancanci haka?,wacce irin qauna ce haka tsakanin nanay da mamminta?. "Jininmu da darajarmu giiftii.........ki riqemin muhammad kawai irin riqon da uwa zata yiwa d'anta" Nanay din ta fada da rauni sosai cikin idanunta. Nauyi maganan itama tayi mata,sai nanay ta zare idonta tana maidawa wani sashen,kamar yadda al'adar hadimansu yake,sunsan komai a sanda ya dace su yishi basai iyayen gidansu sun buqata ba.......wata hadima jakadiya ta matso dauke da wani lullubabben faranti. Idanun saamee fes a kan farantin,har zuwa sanda Nanay ta bakadeshi,take tayi ido biyu da mayafin nanay din. Wani mayafi ne me tsananin daraja a idanun nanay din.....mayafi mafi girman tarihi tsada da qauna a gurinta. Irinsa uku ne da ita,wanda duk tsadarsa bata yafashi,ta ajiyeshi kawai a gurin ajiya na musamman cikin kulawa. Tsakanin hasnaa da balqees data aurar,ba wanda baiso ta bashi shi ya tafi dashi gidansa ba amma ta qiya,sai gashi a yanzun.....a gaban idanunta taga ya daukeshi,ta wareshi,ta kuma lullubawa Akhnan shi. "An rufeki da darajarmu......kina qarqashin kariyarmu" Jakadiyar ta furta cikin girmamawa,wanda tana daya daya cikin mutanen da sukasan darajar mayafin a tattare da nanay din. Idanunta saamee ta janye tana kullesu saboda ruwan hawayen da taji suna neman yi mata ba zata sanda su rumaisa ke dariya qasa qasa cike da farinciki. "Shikenan wallahi,an samu me qwace matsayin captain obbo.......Allah giiftii ta zartashi yanzun dai a zuciyar nanay" Giiftii " Ta sake maimaita sunan a ranta. Bawai suna kawai nanay ta bata ba......wata irin daraja ce,ta dagata sama da sauran dukka matan Ethiopia gaba daya.....darajar da sai da akayi shelar dimbin mutane kafin a mallaka mata ita. Ba suna kawai Nanay ta bata ba,matsayi ne da har abada bazai tabe zame mata ba. Kadan kadan mutane suka fara raguwa,sai mata mafi kusanci na qwarai ga nanay da motii. Sauya hall akayi,wannan hall din yasha banban da wancan,wannan din an yishi ne cikin yanayin da zai bada daman cin abinci ga kowa a sake. Ba jimawa aka shigo da wani babban tray,wanda kallo daya saamee tayi masa wani murmushi ya subuce mata. Farinciki ne fal fuskarta da wani boyayyen murmushi,kamar ba ita bace a mintunan dazu take fakar idanu tana tsane hawayen fusarta da gefan lallausan mayafinta ba.. Kai tsaye aka wuce da farantin gaban Akhnan din. Ta daga idanu a nutse tana kallon yadda aka jera qananun cups masu qaramin faranti daga qasansa dauke da wannan coffee din na asalin noman qasar oromo.....wannan coffee din da zuwa yanzu batajin akwai wani coffee daya kaishi dadin d'an d'ano saman harshenta. A jere suke da wani irin tsari da zai burge me kallo.....to amma ita.....batasan me zatayi dashi ba. "Gabatarwa......zaki gabatar da irin taki girmamawar zuwa ga baqinmu masu girma.....manya masu matsayi a gurin nanay dama masarautarmu....muna buqatar ganin taki qwarewar" Saamee ta furta a hankali tana sakin murmushi. Daga inda nanay take tana jin dadi ne,a nata zaton bayani saamee din ke mata wanda zata fahimta,don haka cikin murmushi take kallo Akhnan din. Wani abune ya motsa a zuciyar Akhnan din,a nutse ta waiwaya sashen da saamee din ke zaune tana zube mata blue eyes dinnan nata masu daukan hankali. Tun bata shaidata......har ta fara shaidata. Yarinyar da akwanakin da tayi tare da nanay ita kadai ke matsanta shigowa gurinsu da tarin hidima da maganganu na kulawa akan haisam. "Nanay captain sheikh bai shigo ba......nanay abincin captain sheikh......nanay coffee din captain sheikh......nanay captain sheik yayi baqi....me za'a kai musu......nanay ruwan zafi.....bazaisha girkin hadimai ba" Sannu a hankali sai abun ya fara mata wani irin. Bata da wata magana ta daban saita captain sheikh,duk wani da'irar maganarta a nan take qarewa,bata sauya suna ballantana wanda kulawarta take kai. Ta dauka ba zataji komai ba......ta dauka ba zataji wani sauyi daga zuciyarta ba.....to amma a hankali sai ta samu kanta da fara jin wani abu yana matse zuciyarta a duk sanda ta shigo ta ambaci sunansa. Bata tana d'aga kai ta kalleta ba sai a shekaran jiya.....shekaran jiya da tazo tana fadin.. "Kamar Captain baya da lafiya nanay........naga Dr Aawel ya fito daga sassansa" "Zan bincika" Nanay ta fadi kaman yadda ta saba amsawa saamee da duk maganan da tazo da ita inde akan haisam dinne a taqaice,bata kuma bari aci gaba da yinta. Abu na farko daya dasa zargi a ranta,sanda ta daga kan don ganin wacece wannan da maganarta kullum iri daya ce?,kuma akan mutum daya?,sai ta samu idanuwan yarinyar suma suna kanta,saidai kuma wani kallo take mata da yake nuna a sace take kallonta. Suna hada idanu Akhnan din ta dauke kai tana maida idanunta kan bowl din da nanay ta kawo mata me cike da wata irin dahuwar wani nama da batasan naman meye ba. Tana jinta sanda take takawa tana fita,haka kawai taji wani abu ya mata tsaye a wuya. Me yasa batasan komai akansa ba sai wata?. Me yasa take satar kallonta irin haka?. Duka duka saamee din kimarta da zatinta a kallon data mata da kuma nata idanun bata wuce irin nasu birra ko bara'atu ba. Bata da wannan haibar sam irin wanda takan hanga tattare dangane dasu rumaisa,hatta da noorah ma,duk da ta gabatar mata da kanta a matsayin qanwar sheikh haisam kamar sauran......amma a yau data daga kai ta kalleta sosai daban take ganinta a cikinsu. "Zo" Nanay ta kirata da tattausan murmushi da kuma yanayi na qarfafa gwiwa. Tsam ta miqe,tana takawa a nutse tana nufar nanay. Miqewa tsaye tayi,tana duban farantin da jakadiyar ta biyo Akhnan dashi. "Ki shayar da baqinmu da hannunki" A hankali Akhnan ta gyada kai,saidai can qasan zuciyarta wani abu daban yana harba mata. Ba shayar da baqinsu bane manufar,abinda tafi fuskanta shine......anason auna karamcinta ne. Idanun Nanay data kalla sun nuna mata komai.....taga kuma yarda da ita da yarda da halinta dari bisa dari cikin idanun Nanay,don haka ta soma takawa a hankali. (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) Da idanu saamee tabi takunta,ba yau ne ta fara ganin takun tafiyarta ba......amma kuma duk sanda zata kalli takun sai ya kwance mata wani abu cikin kanta. Tana takawa ne majestically......da wani irin yanayi da burgewa a takun yake tasirantuwa cikin kanta,amma kuma wannan halittar ta KISHI take wancakalar da wannam daga idanunta. "Jin kai ne kawai da girman kai" Shine abinda take bawa duk wani motsi na Akhnan din da takunta. Tana sane,tana kuma lissafe a kwana goma sha hudun data dauka tana shiga dakin da maganar haisam akan harshenta bata taba daga idanunta ta kalleta ko sau daya ba......hakan kuma bawai yana nuna kara ko alkunya ba,ko kuma batajin abinda take magana a kai a dukka kwanakin,aah......tana lura da ita. Wani irin izza gareta.....tarin dagawa da girman kai data lura bada kowa take doguwar magana ba. Sai a dazun da taje da batun baida lafiyan. Ba rashin lafiyar ya sanya ta kalleta ba.....qilan yadda take maganan ne kamar zata saki kuka. Wani abu tayi.....wani abu da bata taba yinsa ba kaf tsahon rayuwarta illa ga mutum daya wato SULTANE. Kujera kujera ta dinga bi cikin nuna girmamawa ta miqawa dattawan cup din bayan ta tabbatar kowanne ta cikashi. "Allah yayi miki albarka" Suka dinga furtawa ga duk wanda ta miqawa. Wani irin dadi ta dinga ji tun kafin ta gama,can qasan ranta takejin wani irin farinciki. Har cikin jikinta takejin addu'ar tana ratsata "Haka bakin babba yake akan yaro?" Ta dinga fadi can qasan zuciyarta. Tunda take ita ake miqowa.....tunda take ita akewa hidima,yau sai gashi tayi qanqanuwar hidimar da aka tara mata tulin albarkar da batasan yawanta ba. Sanda take komawa mazauninta sai hankalinta ya lula can wata duniyar. Sanda tana da shekaru goma a duniya......sabda morsa safiyya ke tattara mabuqata dattawa a duk ranar juma'a. A jerasu tasa a daukota ta dinga binsu da sadakar kudi da abinci kamar haka suna sanya mata albarka. Abun yana mata dadi a sannan,haka kawai ba tare da itama tasan dalili ba,amma daga randa mammina ta fahimta saita soma sukar abun,a hankali sai abun ya fara fice mata daga rai,ta bijire ta kuma daina zuwa din,hakanan morsa safiyya ta haqura ta sanya hairaan taci gaba har zuwa sanda aka aurar da ita. Cikin wata Royal buggy suke tafiya a nutse cikin hanyoyin masarautar. Wata qaramar mota da ta sake sanyawa Akhnan sallama irin ikon masarautar. Tana da tsananin kyau da daukan hankali,a bude take da wani irin yanayi dake nuna iko da isa. "Zamu qarasa mu duba muhammad" Nanay tace da Akhnan dake zaune a gefanta. Batace komai ba,ta danyi qasa kawai da kanta,haka kawai taji zuciyarta tana tsalle,tana motsawa a nutse da wani yanayi data jima bata jishi ba. Cikin qasaitaccen parlor din nasa da yake da wasu irin views har guda uku,wannan ya bashi wani irin tsari haske me kyau da kuma hangen qawatattun tsirrai data lura kamar a nan aka haliccesu. Wasu irin furanni da flowers masu kalolin dake daukan hankali,furannin da kana iya jiyo mabanbantan qamshinsu daga cikin parlor din. Duk da kanta a qasa yake,amma hakan bai hanata fahimtar tarin banbancin da bangaren da yake dashi ba da dukkan sauran sassa na gidan. Tun daga yanayin tsari da tsarin shiga na security da hadimai dake kai kawo a sassan,yanayin sanyinsa da wani irin lallausan qamshi da iskar sashen gaba daya take bayarwa tamkar an halicci wata qaramae aljanna ce cikin gidan. Daidai da qasan sashen da takalmanta ke takawa tamkar gaya mata suke "Barka da zuwa wani sashe na musamman" Komai na sashen cikin wata nutsuwa yake,daidai da iska da shuke shuken da suke cikin sassan sai take ganin tamkar su kansu nutsuwa ta ratsasu,kamaar akwai wata tarbiyya ta daban tattare dasu. Tun kafin sukai doorstep din ta fahimci akwai wani babban baqo cikin parlor din,akwai wani me girma dake zaune a ciki,saboda yawan adadin dogarai dake zagaye da kowanne taku na sassan nasa. Tana daga gefan nanay sanda suke sallama cikin parlor din. Su biyu ne rak a ciki,wanda kafin ka qaraso zaka dauka tarin mutane ne a ciki,amma haiba da kwarjinin mutane biyun dake dakin a idanun Akhnan sai taji kaman a cike dakin yake. Haisam.....wanda a kansa idanunta suka fara sauka. Wani irin sauka a hankali tamkar fadowar ganye daga jikin reshen bishiya zuwa qasa. Cikin ba zata nashi idanun suka nutse cikin nata. *zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 08187255862 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 08187255862 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 66* Sanye yake da short sleeve leaf green t.shirt,sai dogon trouser nude color daya dan ciza kadan. Wannan sassalkan gashin nasa yana warwatse saman kansa da wani irin yanayi da zai tabbatar maka baiyi tajeshi ya kuma kwantar dashi yadda ya saba ba. Manyan idanun nan nasa sun rusuna kadan da wani irin yanayi daya canza launinsu,rusunawar da sukayi ta qara musu wani irin kyau,ta kuma sake kusantar da eyelashes dinsa na qasa dana sama da suke da tsaho sosai kaman zasu hade. Kallo ne na sakanni,saidai ya tafi da wani irin yanayi da saqo da batasan ya fita a idanunta ba. Wani irin kyau.....kwantaccen kyan nan me sanyi da wani irin sassanyar nutsuwa take hanga a tattare da fuskar nan ma'abociyar haiba. Fuskar data kwashe darare tana kawo mata farmaki cikin mafarkinta, fuskar data kwashe kwanaki tana juyi saman tattausan gadonta tana gilmawa ta cikin duhun dakinta....fuskar da sannu a hankali kewarta ta fara illatata ba tare da ta farga ba. Wani sassanyan aniyar zuciya ta qwace mata,taimakonta daya ta sauka ne a hankali daga zuciyarta zuwa hunhunta ta fidda siririyar iskar ta hancinta. Idan har taga daidai.....wani abu taga ya hadiya a hankali,ya kuma motsa bakinsa kadan kaman zaiyi magana,sai kuma taga ya zare idanunsa daga kanta. Kan motii ya maida dubansa,wanda yake zaune dab dashi saman wani ottoman lallausan offwhite. Kallo daya tak yayi mata wani abu ya tsarga masa,tun daga tsakiyar kansa zuwa tafin qafarsa yaji kaman yana neman loosing control nasa,baya buqatar hakan kuma,a yanzun da yake gaban motii da kuma nanay. Baisan abun zai zame masa jarrabawa ba sai daya gaza samun ganinta na wadannan kwanaki. A duk inda zai sanya hannunsa sai yaji bai ajesu daidai ba. Kaf pillows dinsa na saman gado ba wanda baisha matsa ba.....amma still baya samun sassaucikoda na daqiqa daya. Ya sauya pillows ya sake qara wasu amma still ba wani taimako da yake samu. Baisan daga inda matsalar take ba..... Hirar su ta shekaran jiya yake tunawa. Shi da maleek da suke turkey yanzu haka shida falaaq din,sai naseeb. Hirar ta ranar iya su uku ne,don naseeb yace iya hirar masu iyali ce kawai,saidai shi dimma daga qarshe shuru ya musu tsakanin naseeb da maleek suketa shaqiyancinsu. Ya sani,wani abun idan maleek ya fada dashi yake,maganan maleek ta qarshe ta sanyashi yanke kiran ba tare da yace musu komai ba,sukayita qoqari sake kiransa amma yaqi basu wannan damar. A daren idanunsa ya maida ya lumshe yana jin yadda ciwon ke sake masa qarfi. Baisan dalili ba,amma har bayason dare yayi cikin kwanakin nan. Tun yana irga kwana daya biyu uku har zuwa sati guda. Yayita zuwa gurin nanay dukka satin,zuwan dashi karan kansa baisan dalilin yinsa ba. Yakan jima zaune yana jiran nanay,yakan jima zaune suna hira dashi. A satin ya dauka zaiga koda gilmawarta,a satin ya dauka ko sau daya zasu hadu gurin cin abinci a gurin nanay amma ba koda alamunta,sai saamee dake neman kusanci dashi. Basai an gaya masa ba.....a matsayinsa da matakin karatunsa.....tabbas akwai wani gagarumim sauyi dake neman zuciyarsa idanu rufe,saidai ya gaza samun qwaqwarar hujja ko shaida da zai gasgata hakan. A yanzun da idanunsa suka sauka a kanta.....a yanzun da take takowa zuwa cikin parlor din.....idanunsa basa kanta.....amma cikin jininsa da jikinsa yakejin takunta....cikin jininsa da jikinsa yakejin wannan kusancin. Yana jin kamar wani abu daya rasa ne yake takowa zuwa gareshi,yana jin kamar wani sashe na jikinsa da aka cire aka wurgar ne yake dawowa zuwa anihin jikinsa. Nauyi da kunyar mootii takeji,wani irin nauyi da ko sultane batajin nauyinsa haka. Ta wani sashen sai take ganin wasu kamaceceniyar yanayi da dabi'u a tsakaninsu. Cikin girmamawa ta isa gabansa,ta zube a hankali tana gaidashi da harshen oromo data fara kama kalmomi da yawa na kurkusa,kaman gaisuwa da sauransu. Da murmushin nan me cike da dattako da kulawa ya amsa mata "Anya khadeejatu?.....har yanzu baku gama bidi'o'in naku ba?" Mootii ya fadi sanda Akhnan ke isa gaban gadon haisam din,sai kuma ta samu Nanay ta ja mata kujerar dake dab dashi din. Wani abu guda daya data lura dashi,komai na nanay ya ta'allaqa ne akan yadda zata bawa haisam kulawa.....kamar yadda tata kulawar kuma a yanzun dukka ta tattareta a kanta. A kunyace ta zauna,saidai abinda ya bata relief janyewar nanay a nutse ta koma kusa da mootii daya koma kujerar can kusa da qofa yana riqe da wasu takardu a hannunsa,wannan ya haifar da tazara a tsakaninsu,don parlor ne me girma qwarai. Idanunta ta daga zuwa kan fusarsa,saidai gaba daya kalaman bakinta sun maqale saboda samun lumsassun idanunsa da tayi a kanta. A hankali ta maida bakinta ta rufe,ya riga ya saukar mata da wannan dafin.....ya riga ya luguiguita zuciyarta da wadannan narkakkun idanun nasa da suka sake narkewa. "Kwananki nawa da sanin bani da lafiya?" Ya furta softly saidai tana jin wani abu can cikin sautinsa. Samun kanta tayi dayin qasa da kanta,tana jin wani kimarsa tana tabata sosai. A yanzun wani kallo na daban take masa.....ba don dukiyarsa ko.matsayinsa ba.....aah,sai don yadda ta samu ahalinsa da sanin ma'anar GIRMA da MUTUNTAWA. "Kwana uku" Ta furta a hankali da siraran labbansa da yaji kaman ya miqa yatsunsa a shafesu a hankali. Kai ya jinjina a hankali,yana jin yadda gaba daya jijiyoyin jikinsa suke narkewa. Qamshinta.......shigarta da yanayinta gaba daya. Kwana sha hudun yake sake maimaitawa cikin kansa. A kwanakin ya dinga jin wani abune yana masa yawo a kai,a kwanakin ya tuna duk wani memories nashi da ita tas.....ba abinda ya manta tun daga zamansu a agadez zuwa ganinsa da ita na qarshe. A kwanakin ya dinga jin wani abu yana yawo da zuciyarsa cikin wani irin yanayi. Duk debe kewa da library da litattafansa ke masa a wannan lokacin su gaza dauke masa komai. "Kwana uku?" Ya maimaita a hankali kaman wanda kwanakin sukayiwa zuciyarsa nauyi. Fuskarta ta narke a hankali,tana jin kamar bata kyauta ba......tana jin kamar abun bai dace ba. "Bahaushe yace gaida me gaidaka ko?" Can wani sashe na zuciyarta ya tunasar da ita. Ta tuna yadda yake kula da ita duk sanda wani ciwo ko rauni ya sameta.....a saudiyya....a festival d'l'Aîr. Baiyi bacci ba... Bai samu sukuni ba sai data samu......amma ita yanzu?.....sau daya tak ta kasa gwada masa halaccinta?. ".....ko sau daya...." Ya sake fadi a hankali da wani irin coolness idanunsa cikin nata.....yana jin wani abu me qarfi yana fusgarsa. (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) ".....baki nemeni ba?" Ya qarashe da sigar tambayar data sanyata lumshe ido tana jan wani numfashi. Shigar kalmar data gauraya da sautinsa cikin kunnenta.....wani irin lallausan sauti da takejin kamar ba muryarsa ba....kamar ya manta waye da waye a gurin. "An hanani....." "Na sani....." Ya tari numfashinta ba tare daya bari ta qarasa ba. "Nanay ko?" Ya sake fadi da wani nauyi cikin muryarsa. Sai ya maida bayansa ya jingina sosai da fuskar kujerar. "Me yasa rashin zuwana ya masa ciwo?" Ta tambayi kanta da kanta cikin jikinta har yanzu da idanunsa a kanta. Da zai taimaketa....da zaiyuwu daya debe wadannan tsimammun idanun nasa daga kanta,rikitata yake.....sosai yake sanyata jin tana rikicewa. "Ko sau daya....ko da tambaya?...koda saqo?.....koda daga bakin qofa ne?" Ya sake fadi da wani lallausan sauti me cike da tuhuma. Kaman zata shide taji,don sai taji muryar tasa tayi wani mugun kusa dashi,kuma koda data motsa saita fahimci ya rage distance din dake tsakaninsu ne. "Don Allah......kayi haquri" Ta fada a rarrabe tana jin wani kunya da nauyin kusancin daya samar a tsakaninsu. Kamar idanunsa baya tuna masa nanay da motii dake gurin?. "Ba komai" Ya fada a hankali yana sake relaxing sosai cikin kujerar karo na biyu,sannan ya maida idanunsa ya lumshe. Har cikin zuciyarta takejin bata kyauta ba.....amma da wanne harshe.....da wannw yanayi zata cewa nanay GANINSA NAKESON YI?. Da wanne idanu zata cewa nanay KEWARSA NAKE?. Tayi imanin baisan abinda takeji cikin zuciyarta ba.....inda ya sani bazai tuhumeta da komai ba. "Da nine.....da sai a kiramin bappi ko?". " Kayi haquri naceeeee" Ta furta da sauri a wani mugun narke da wata irin shagwaba da bata yita da kowacce manufa ba....illa manufar yabar zancan haka. Yanayin ya sanyashi cije lips dinsa na qasa a hankali yana lumshe idanunsa. A hankali bakinsa ya furta! "Ya salam" A hankali yana jin yadda juriyarsa take zagwanyewa....a hankali yana jin yadda dauriyarsa take raguwa. Anya zai iya?....zai iya ci gaba a haka?,alhalin tana gefansa?......zai.iya ci gaba da qaryata kansa?......alhalin komai yana bayyana gaskiyar abinda yakeji?. Cikin cikakkiyar nutsuwa mutumin yayi sallama. Dogo ne baqi me murjajjen jiki,wanda asalin fatarsa ta nuna qabilar Ethiopia ne na gaske shi din. "Allah ya taimakeka....na kammala" "Madalla Dr jamaal.....ina saurarenka" Motii ya fadi,bayan ya baiwa Dr jamaal hankalinsa. Takardar hannunsa ya bude yana sake kallonta,sannan ya rufeta a hankali,ya maida dubansa ga haisam dake zaune,da Akhnan dake gefansa,sannan ya maida dubansa ga motii. "Ranka ya dade.....kaman yallabai yayi aure ko?" Ya fada cikin girmamawa da d'ari d'ari,kasancewar sarai yasan halin haisam. Tambayar kuwa ta sauka saman zuciyar haisam din,sai yaji kaman duk duniya Akhnan din yake kalla tun daga shigowarsa. A nutse ya matsa yatsunsa,muryarsa can qasa taji ya furta. "Tashi ki shiga ciki" Daga kanta tayi a nutse,cikin yanayi na rashin fahimta,saidai ba tare daya kalleta ba ya sake maimaitawa. "Jeki giiftii" Nanay ta furta a nutse. Miqewa tayi a hankali,tana jin wata kunya na dabaibayeta. Mene zaice ta wuce ciki?,bedroom dinsa fa kenan?,a gabansu?,bayajin nauyi ne?,ita bataga dr din ya kalleta ba kwata kwata,yaushe ma yaga hakan shi?. Shuru parlor din ya dauka har zuwa sanda Akhnan ta bace cikin dogon corridor din da zai sadata da lafiyayyun royal master bedrooms dinsa guda hudu. "Me ya faru.......muna jinka" Motii ya fada yana duban Dr jamaal. Dan shafa kansa kadan Dr jamaal yayi,akwai wani kwarjini da motii din yake masa,duk da kasancewarsa kusan uba a gurinsa,saboda shi din yayan mahaifiyarsa ne. "Irin dai wancan ciwon da yakeyi lokaci bayan lokaci.....so zuwa yanzu ya kamata ace ya rabu dashi,tunda akwai aure a......" Kasa qarasawa Dr jamaal din yayi,saboda wani kallo da haisam ya watsa masa. Sosai yake qunshe dariyarsa ta yadda motii bazai gaji ba,da idanu kuma yakewa haisam din maganar "Taimakonka nayi". Shuru ya wanzu a falon yana hadewa da sauran maganae Dr jamaal data maqale bai iya qarasata ba. " Na fahimta.....na fahimta " Motii kawai ya maimaita har sau biyu yana gyada kai. Ba shiri Dr jamaal ya miqe yana shafa kansa. "Ga magungunan da zaiyi amfani dasu nan,saidai su din relief kawai zasu bashi......Allah ya qara lafiya" Ya fadi yana karkatawa inda haisam ke zaune,nauyin motii da nanay yana narkar da shi. Bai amsawa jamaal din ba,sai tsarabar harara daya sake aike masa,yana boye da dariyarsa ya fara takawa yana fita motii da nanay na masa ya gaida gida. Kaman jira motii yake jamaal din ya fita,sai shima ya miqe tsam yana fadin. "Kinga yanzun ai sai ki bashi matarsa ko?" "Zatayi jinyarsa ne yasha magungunansa motii,kwana hudu ya rage mu kammala a rakata gidanta.......ko zuwa da safe kaji qwarin jikinka......zan karbeta mu qarasa aikinmu" Ta fada tana dan duban haisam din. Saidai itama ta kasa duban cikin idanunsa.....ta daure fuska kawai tana rattaba bayani. Murmushi kawai motii yayi yana takawa zuwa bakin qofar da zata fiddashi daga parlor din ba tare daya sake cewa komai ba. Ita dinma saita zabura tabi bayan mijinta,saidai tana sake jaddadawa haisam aron Akhnan din ta bashi. Can qasan ran motii dariya kawai yayi, "wanne irin qarfin hali ne wannan khadeeja?,mutum da matarsa sannan ace aro aka bashi?" "Eh.....shi akewa gatan ai,kuma me yaci kwana uku?,kwana kin al'ada basu cika ba" "K'nnnnn,to Allah ya taimaka" Abinda motii ya fadi kawai kenan,can qasan ransa yana sake jinjinawa halin mata,lallai halin mata daban yake dana maza,amma zaibar nanay din ta gani ganin idanunta,shidai zaiga ta yadda zata saka shinge tsakanin lafiyayyen yaronsa da halalinsa. Yaron da kallon mata ma bai iya ba ballantana doguwar magana.....yanzun ga maganinsa ta saka dokar sai bayan kwana uku?. *_to masu karatu.....nima dai nacw maji ma gani wai an binne tsohuwa da ranta😂,dama ana bawa kura ajiyar nama?,to qila sheikh dinmu na mutunci dai yasan darajar abun aro,zai kuma riqeshi da kyau.....mu hadu daku a ranar litinin in sha Allah_* *_har kullum_* *_Hugumanku ce_*🙌🏽 *zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 08187255862 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 08187255862 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 67* A hankali take daga qafafuwanta tana sauke qafafunta saman tattausan carpet din dake malale cikin dakin. Idanunta take watsawa a hankali zuwa ga kowanne sashe dake dakin wanda yake fidda wani irin tattausan qamshi da wani sanyi da yanayinsa yasha banban dana parlor din data fito. A hankali zuciyarta ke bugawa a qirjinta qamshin da nutsatsen yanayin da dakin yake fiddawa yana ratsa zuciyarta da gangar jikinta gaba daya. Idan tace iyakar rayuwarta.....iyara adadin yadda ta rayu a duniyarta bata ganin daki me tsari da daukan hankali irin wannan ba batayi qarya ba. Cak ta tsaya tana tsoron wani abu,tsoron qauyanci......tana ji a hankali kaman tana neman daburcewa da rasa dukkan wayewar da take da ita. Uwa uba wani baqunta takeji sosai a jikinta,ta sake zuqar iska sosai zuwa hunhunta wadda ta kasance wata irin sassanyar iska dake cakude da qamshin turarennan nasa da batajin har abada zata daina sonshi......turaren data shafe a mayafinta tun ranar da aka shigo da ita cikin gidan,ya kuma zame mata wani abu daban na debe kewa.. Bayan wannan qamshin,wani launin qamshi ne daban da bazata iya banbanceshi ba suka cakuda suka bada wani kalar launin qamshi me saukar da wani irin yanayi daban ga zuciya da gangar jiki. "Komai nasa.....komai nasa me sanyi ne....komai nasa na dabanne.....komai nasa yana fadin cewa shi din......" Saita kasa qarasawa tana bude idanunta a hankali,wani nau'in tuhuma yana fitowa daga qasan zuciyarta. "Me yasa yake tsayemin har haka a zuciyata?,me yasa komai nasa yake burgeni?.....me yasa komai nasa yakemin nauyi da kuma kwarjini?" Ta tambayi kanta tana komawa da baya a hankali ta zauna saman lafiyayyar sofa din dake ajiye wani sashe daban na dakin,wadda tayi matuqar dacewa da launin dakin da tsarinsa. Idanunta suka sauka a hankali akwan wani sashe dake dakin. Akwai wani dan ado da qawata gurin,darduma qur'ani carbi da wasu launikan fitilu masu kyau maqale agurin,wasu kuma a ajjiye a qasa,sai litattafai 'yan tsiraru da basu da yawa. Tattausan murmushi ya subuce mata,batasan wacce irin soyayya bace tsakaninsa da karance karance na addini ba. Zai wahala ya wanzu a guri bakaga tasirin wani abu daya shafi addini a tare dashi ko litattafan addinin ba. Tayi kaman zata miqe don isa ga litattafan ta duba wanne iri ne,don tun daga sanda ta karanta tarihin manzan Allah take nutsawa da kadan kadan cikin litattafan addini na tarihin annabi da sahabbansa,saboda wani irin nishadi take samu qarin ilimi da dawo mata da wata rayuwa ta shekaru dubunnai da bata wanze a doron duniya zuwa gabanta. *N A N A Y* Cikin wani irin yanayi,wani irin tattaki da dama sun riga sun saba lokaci lokaci sukanyi tsakaninta da motii cikin masarautar suke takawa zuwa ga sashen nanay din dake manne dana motii din. Shuru Nanay ta samu kanta dayi,ba kuma don tsokanarta da motii kawai yakeyi ba.....aah,hankalinta ne taji a hankali yana kaiwa kan maganganun motii din. "Zanga yadda wannan rigimar zata qare khadeeja,haka akeyi tsakani da Allah?,yaro da matarsa?,mema kuke jira?". Can qasan ranta tana jin akhnan din tamkar daya daga cikinsu balqees ko hasnaaa ce. Akwai wani irin narkakken tausayin yarinyar da takeji yana danqare qasan ranta. Duk da har yanzu basu samu zama haisam ya fede mata meye da meye ya faru da safiyya da safeena ba......amma tana ji a jikinta akwai abubuwa masu tsananin nauyi.....akwai abubuwa masu tarin yawa da sukazo suka dinga faruwa suna shudewa. Akwai abubuwa da yawa.....da dama masu tarin gaske da take karanta tattare da akhnan din. Har cikin jininta take qaunarta,irin qaunar nan dai da takewa safiyya da safeena. Tana tsananin son safeena......tana tsananin son safiyya,hakanan a yanzu take shauqin son ganin safiyyan data rage mata,saidai batasan dalilin da yasa haisam din daya kawo mata su ya debi wani lokaci da zai sadata da safiyyan ba. Amma koma meye ta sani,haisam din wani irin nutsatsen yaro ne me tsari,kyauta daga Allah daya zame mata abun alfahari,ba'a gareta kawai ba,har a gurin danginsa na uwa da uba dama 'yan uwansa gaba daya,ta tabbatar akwai babban dalilin daya sanyashi haka. Can qasan ranta takejin wani abu me kama da tausayin akhnan,haisam d'anta ne....d'a mafi soyuwa a gareta,zataso ya samu dukkan nutsuwa daga gurin mace ta gari,zataso ya samu dukkan kwanciyar hankali irin wanda kowanne d'a namiji daya dace yake samu,wannan shine babban dalilin daya sanya takarkatar da dukka wadannan kwanakin gurin koyawa akhnan din basic abubuwa da zata kula da mijinta da kanta. Ta lura akwai abubuwa da yawa da bata iya ba,baata saba ba,batasan ma yadda zata yiwa kanta ba ballantana waninta. Ta sani su irin wadannan abubuwan mace ko ke wace,duk gatanki....duk matsayinki inde zaman aure zakiyi baki da wata daraja idan baki sansu ba,baki da wata daraja idan baki koyesu ba,baki da wata daraja idan baki iyasu ba. A yanayi rayuwar akhnan din,ta karanci akwai gibi da yawa. Ita karan kanta taimaka mata ake gurin kula da kanta,batasan yadda zata yiwa kanta hidima ba bare waninta. Ta kwashe dukkan lokacinta,ta bata wuninta da dararenta wajen mata wasu karatuttuka,tana kuma fata ko yaya su amfaneta. Ta sauke ajiyar zuciya tausayinta yana sake ratsata. Indai har haisam ya gaza jurewa ya taba akhnan din,ta sani ba zataji da dadi ba. Tayi imanin zataji a jikinta ainun. Tafi kowa sanin waye yaronta.....tafi kuma kowa sanin yaqin data shiga shima ya shiga gurin kare kansa da mutuncinsa. Da gaske ne....kuma gaskiya motii ya fada a yanzun. A yanayin haisam din zai wahala a irin wannan yanayin na kadaicewa tsakaninsa da halalinsa ace Akhnan din takai labari,amma kuma sai ta tuna wani abu guda daya bata relief. Akhnan din period takeyi,duk da batasan yaushe ta fara ba,kuma yaushe zata gama ba,amma tabbas tasan bata da tsarki,ko wannan zai taimaka ta tsallake wannan tarkon?. Abinka da uwa,haka nan kuma sai taji tausayin haisam ya maye gurbin zulluminta da fargabarta. Abune mai wahala namiji lafiyayye irin haisam din.....ya iya sanya idanunsa akan halittar akhnan baiji komai ba. Abune me wahala namiji cikakke ya iya kallon akhnan ya dauke idanunsa a kanta cikin sauqi. Ba namiji kawai ba.....ita kanta data kasance d'iya a gurinta idan ta kalleta tana maimaita kallonta a kanta ne. Sau tari takan furta. "Subhanallah" Ko kuma "Fatabarakallahu ahsanul khaliqeen". Wani irin zubin halitta me kyau da tsari Allah yayi mata,wani lokaci sai ta dinga hangen wani bangaren kyau da ake wassafa matan aljanna dashi,kaman dogon wuya,tsayayyun breast kuma masu yalwa da tudu da sauransu. Ta sani sam bata isa ta hada kanta da matan aljanna ba......amma wasu siffofi na kyay ta san ta hadasu,koda ba dari bisa dari ba,to casa'in da tara ne bisa dari. "Nanay.....ina giiftii" Noorah data shigo riqe da camera dinta da itace cikakkiyar abokiya kuma qawarta ta fada tana duban nanay dake shigowa a lokacin sassan nata,bayan ta yiwa motii tattaki zuwa inda motocinsa suke jiransa zai wuce wani taron saukar qur'ani. (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) Tambayar ta yiwa saamee daidai,sai taji noorah ta matuqar bugeta da tayi tambayar. Tambayar da take ranta kenan noorah din ta wakilceta,tambayar da tasan ba zata iya yiwa nanay ita kanta tsaye ba,don tana kula da duk wani abu da zatayi da nanay zata iya gani kai tsaye wanda zai tuna mata da zarginta na Kamar tana son muhamamd haisam din,har komai da zatayi ma ya dasa tunanin kishi takeyi da akhnan. Da nanay ta daga idanunta ta kalli su rumaisa sai taga kusan dukkaninsu kamar tambayar da noorah tayi mata itace a bakunansu,kawai noorah din ta wakilcesu ne. Murmushi ta saki kadan,wani irin qauna suke gwada mata data juye zuwa wani irin sabo da shaquwa. Sabon daya shiga tsakaninsu zaka dauka dukkaninsu ita ta haifesu,duk da kasancewar akhnan din ba ma'abociyar surutu ba,tana zama kawai a cikinsu tana jin hirarrakinsu da harshen oromo da a yanzun ta iya kaso ashirin da biyar cikin dari. Zata yi murmushi sau tari idan sukayi wani abun,maganarta qalilance,bame yawa ba amma me tarin ma'ana. "Tana girin obbo dinku.....na barta ta kula dashi" Ta amsawa noorah tana amsar wayarta daga hannun jakadiyarta zuhura. Wani irin duka kalmar tayi mata tana jin kamar ana girgizar qasa saman kanta. Spoon din abincin data debo ta maidashi a hankali tana ajiyeshi,tana jin wani irin abu yana tsaga zuciyarta da qirjinta kamar iskar dake kai kawo a gurin ta mata kadan. Ji tayi kaman nanay tana sane ta fadi maganan kai tsaye.....cikin wani irin yanayi take magana na nishadi kuma kanta tsaye. Ta yaya zata bari wannan alaqar ta qullu haka da sauri?. Saita miqe a nutse ba tare data bari kowa ya ankara da ita ba ta soma nufar kitchen tana maida farantin abincin. "Ta tafi kenan Nanay?" Noorah ta tambaya tana kwabe fuska,sai nanay tabar danna wayar da takeyi ta maida dubanta kan fuskar noorah din. "Dama batazo don ta zauna damu ba noorah,tana qarasa kwanakinta da saura kwana uku suka rage zata wuce gidanta ita da obbo din naku" Idanu noorah ta fidda. "Nanay......harda obbo shima?" "Eh mana....." Ta amsa mata tana tsare noorah din da ido. Shuru ta danyi sai kuma ya furta "K'nnnn" Tana maida wayarta ta rataya a wuyanta. Tana jin Aanani na mata dariya. "Autancin nan ya cuceki noorah.....kin dauka obbon zai dawwama ne a nan?". Daga kanta rumaisa tayi daga assignment din da takeyi ta kalli Anaani. "Ke kowa ma saikin tsokana ne Anaani?" Dariya abinta Anaani tayi. "Allah banga kyau a autanci ba" Sake jifanta da harara rumaisa tayi. "Ai baiwa ce,tunda Allah bai baki ba saiki zauna a matsayin da kike kai ki haqura hakanan". Murmushi kawai nanay tayi tana miqewa daga gurin. Irin wannan 'yan qananun fadace fadacen nasu ta riga ta saba dashi tun ba yau ba. Kawai abu daya take tunani,duk randa ta aurar dasu shikenan?,shikenan haka gidan zai mata shuru?,shikenan haka zata daina gilmawarsu ta daina jin muryoyinsu?. "Nanay" Taji an kirata a tausashr daga bayanta. A nutse ta waiwaya don bataji alamun akwai wani cikinsu daya biyota ba. Saamee ce,sanye cikin doguwar rigar dake zuwa hade da hijab dinta. Da wannan innocent face din nata me cike da alamun haquri,kamannin da sukayi sak da sak dana mahaifiyarta,babbar hadimarta data zamewa nanay kamar 'yar uwa saboda dadewa da kuma sabo da amana irin ta mahaifiyarta. "Saamee.....ya akayi?,akwai wani abunne?" Nanay ta fadi tana duban saamee da wannan idanun nata na uwa,da wannan yanayin da take iya karantar kowacce buqata ta d'anta. Murmushi kadan saamee tayi,tana jin yadda zuciyarta ke tsalle cikin qirjinta. Tanaso ta roqi wani abune da babu shi cikin al'ada.....amma tana jin karamcin nanay zai sanya tayi mata. Zata roqi wani abune da yake cikin manya manyan tsari da schedule dinta na tsanin cimma nasararta.....tana addu'a da fatan wannan zaren da zata qulla ya dauru a daidai. *zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 08187255862 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 08187255862 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 68* "Cewa nayi....me zai hana wani na cikin gida ya kasance da giiftii safiyya a sashen obbo?.....duk da ya saba da al'ada da tsarin masarauta,amma saboda jagoranci da nuni akan yadda komai yake na sauran abubuwan da bata sani ba ko bata fahimta ba na masarauta. Dole ana buqatar makusanci na captain don muna buqatar sirri akan baqin al'ada dake jikinta su kammala ficewa tas ba wani tabu ko aibu da wani zai kalleta dashi,tana buqatar me mata nuni don kula da captain sosai da samar da qarin kusanci a tsakaninsu.....a duba mata cikin amintattun hadimai.nanay,hakan kamar zai sanya komai yafi zuwa mata da sauqi....amintaccen da zai zama me sirri,ina neman afuwa idan maganata tazo a wata gaba da bai dace ba,ina fatan kuma za'a gafarceni da shishshigin da nayi" Ta fada tana maida kanta qasa sosai ba tare data iya hada idanu da nanay ba. Shuru nanay din tayi,a hankali tana nazartar saamee din. "Wa kike ganin za'a hadata da ita?". "Amintattummu nanay.....zatafi samun sauqi akan abubuwan da bata sani ba batare data tambayi kowa ba". "Zaki iya riqewa da dauke wannan amanar?" Duk da buqatarta kenan,kusantar duk wata mu'amala ta haisam din da akhnan.....duk da burinta kenan amma sai taji kalmar nanay din ta mata nauyi. "Idan akwai wadda ta fini cancanta nanay......ina ganin ita zatafi dacewa da wannan matsayin". "Babu saamee,saboda ke kadai kikayi wannan tunanin,saboda bakyason diyata ta wahala ko ta nemi tallafi daga waje akan abinda ya shafi tsari da al'adarmu,....ke zakije,tare kuma da amanar tsayawa iyakar iyakokinki". Har cikin ranta taji wani sanyi yana saukar mata,KUSANCI shi kadai take buqata a tsakaninsu a yanxu. Tanaso ta qarewa mu'amalarsu kallo ta nazarceta,tasan raunin akhnan,ta soka nata qudurin ta qarqashin wannan raunin. "Na gode da yarda aminta da kikayi dani,in sha Allah......zan kare duk wani muradai da martabarki data obbo dama masarautarmu gaba daya". Kai nanay ta jinjina,tanason gamsar da kanta hukuncin baiyi rashin tsari ba.....kuma ba kuskure a cikinsa. Takawa taci gaba dayi har ta isa daya daga cikin kebantattun dakunan hutawarta,ta lalubi number wayar kai tsaye ta kira,tayi shuru tana jin yadda wayar ke bugawa ta cikin kunnuwanta a hankali. *A K H N A N* Wayarta ce tayi qara a hankali cikin qaramin sound din duka ringing haka suke da wani irin sanyi,ta koma ta zauna a hankali tana duba me kiran. "NANAY" data gani jikin wayar da take amfani da ita tun a wancan ranar da hasnaaa ta bata ya sanyata daidaita zamanta tana shirin daga wayar. Wani kima da kwarjini matar ke mata,wani girmanta da nauyinta take gani cikin idanunta. Bata sani ba,ko wannan hirarrakin da takanji anayi akan surukai normally anajin nauyinsu ne?. To amma ba wannan ba......cikin zuciyarta tana jin wani irin kusanci tsakaninta da nanay,bawai kawai iya kunya bane. Tanajinta da wani irin kusanci da yayi kwatankwaci da kusancin da D'A yakeji tsakaninsa da MAHAIFIYARSA. Da cikakkiyar sallamar da a yanzun ta fara zamewa akhnan dabi'a ta amsa wayar nanay din,cikin sanyi da nutsuwar da takanji ta mamayeta a duk sanda zasuyi magana da nanay. "Giiftii safiyya" Ta kira a nutse. Sunan yana yiwa akhnan wani irin girma da nauyi idan nanay ta kirata dashi,yana tuna mata da abubuwa masu yawan gaske,yana kuma tuna mata da ita wacece. "Na'am nanay" Ta amsa mata a nutsen itama. "Nafito?" Akhnan ta tambaya a hankali,tana fatan Nanay tace eh. Wani irin abu takeji a kowanne sashe na zuciyarta yana danneta da wani irin nauyi da bataso. Wani irin abu da sannu a hankali ta fara zargin SO ne....wannan son dataketa avoiding......wannan son da take qaryatawa.....sannan soyayyar da takejin kunyar tabar zuciyarta tayi amanta. Ta yaya tana mace ita zata fara?. Duka ma wai yaushe tayi saken da wannan abinda takeji din ya juye zuwa soyayya?. Wannan malamin.....malamin nan dai nasu falaaq.....malamin nan dai da takewa kallon bagidaje.....wannan malamin daya shayar da ita mamakin da har yanzu bata gama kwankwadeshi ba. Magajin sarauta a wata duniyar da kullum ta daga kai,....kullum ta daga kai taga irin girma da matsayin daya siya mata.....kullum ta daga kai taga tarin qauna da soyayyar daya siya mata ya jawosu zuwa cikin rayuwarta......kullum ta juya tunaninta tana duban yadda ya kawo wata mace cikin rayuwarta wadda ruhin mahaifiyarta ya koma ga ubangijinsa yana mararinsa......saita rasa ME YA DACE TA BASHI?....ME YA DACE TA SAKA MASA DASHI?. "Ki soshi" Amsar da zuciyarta ke bata kenan aduk sanda ta xurfafa cikin irin wannan tunanin,amma saita juya kan nata a hankali,saita dinga ganin kamar ba a wannan muhallin bane kyautar zuciya.....ba'a daidai wannan lokacin ba.....ba'a wannan yanayin ba sam sam. "Mun wuce ai,dani da motii" Amsar nanay ta shiga kunnuwanta a hankali suka bata wani sauti na faduwar gaba. Sai data qara yawan numfashin da take zuqa zuwa ga hunhunta tana jin wata siririyar fargaba. Zamanta na duk minti daya a nan gurin hatsari ne.....hatsari ne ga zuciyarta gaba daya. Komai da zata kalla nasa.....komai daya shafeshi idan ta kalla sai taji kamar zuciyarta kamar tana sake nutsewa a cikin wani sassanyan ruwa a hankali da wani irin nisan nutsewa. "Giiftii" Nanay ta kirata da sautin da yaja hankalinta sosai. "Na'am nanay". " Na bashi aronki......ki zama kusa da inda yake,ki kula dashi,na kwana uku kawai". Ta fada a nutse amma kaman itama tanason fahimtar wani abu cikin kalamanta data fada din. Wani nauyi taji kaman nanay ta aza mata. Sun tafi sun barta.....sun tafi sun barta a muhallin daba kowa,daga ita saishi. Sun tafi sun barta da wannan sheikh din....wannan malamin dai da yake mata tsananin kwarjini.....sun tafi sun barta da wannan mutumin da a kullum....daga ita sai zuciyarta tasan yadda take gudun fanfalaqi.....yaqi da fadi tashin qaryatawa dama boyewa gami da binne abinda ke cikin ranta da zuciyarta gaba daya. Anya?,tana da qwarin gwiwar jure wannan kusancin?,anya tana da wannan jarumtar?,ta kula dashi?......zata iya?. "Giiftii" Ta sake kiranta. "Amma ba kulawa dashi kadai ba......" Ta fadi tana yanke maganar,ta bawa iska dama a tsakani sannan ta sake cewa. "Ki kula da kanki ma...." Sake jin wani nauyi tayi yana sake daureta sosai. Kunya kuma tana samun kyakkyawan muhalli tana cakudewa da fargaba cikin ranta. (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) "Ki kula dashi da dukka nau'in kulawar data dace......irin kulawar da mace ke bawa mijinta. Karki bari yaga gazawarki duk qanqantarta.....saidai kowacce kulawa tana da iyaka" Ta tsagaita da magana kamar tanason ji ta bangaren akhnan din. "Yana da hali me kyau,bawai don yana yarona bane......kuma idan bashi da lafiya,yana komamin kamar qanqanin yaro ne,wannan din dabi'arsa ce.....tun daga quruciya har zuwa yanzu daya girma bai sauya ba" Wannan kalmar ta nanay ta qarshe tana jin yadda ta furtata,da wani sassanyan murmushi a cikinta......wani kalan murmushi da koda akhnan bata ganshi ba tasan yana tuna mata da wani bangare ne na quruciyarsa,sai taji kaman Nanay taci gaba,kaman nanay tayita bata labari akan abinda ya shafi quruciyarsa. "Giiftii" Ta sake kiran akhnan din a tausashe,kiran daya ratsa har zuciyar akhnan din. Sautin ya isa kunnuwanta da wata irin nutsuwa,tana sake ji kamar tana magana da mamminta ne. "Ko tsakanin harshe da haqori ana sabawa......a kwanaki ukun nan,koda zakiga alamun yana fushi dake....." Saita sake dakatawa,sannan ta dora a hankali. "Ba fushi bane.....kulawace da baya iya boyeta". Wani siririn murmushi ya kubcewa akhnan......murmushin da batasan yadda akayi ta samar dashi a saman fuskarta ba. Maganan nanay ta yanzu.....kalmarta data fada a yanzu,hakan yana nufin......ba fushi yakeyi da ita ba dazu?....hakan yana nufin kulawa ce?. Kenan itama tana cikin jerin sahun mutane masu muhimmanci a gurinsa da zasu iya samun kulawa?. "Idan namiji irinsa yayi shuru......kiji tsoron shurunsa....musamman a inda akayi rashin kyautawa......amma idan yayi magana,wata qofa ce ya bude miki" A hankali ta gyada kanta tamkar tana gaban nanay. A hankali duk wata kalma dake fita daga bakin Nanay ke burgeta......a nutse takejin kowacce kalma daga bakin nanay din tana samun wani kyakkyawan gurbi da matsugunni a ranta. Kamar tana buda mata wani babi ne.....kamar wani kundi me matuqar daraja da muhimmanci take buda mata. "Yana da wata zuciya da take MAKAHON SO...qila shi yasa Allah ya damqa masa 'yar uwarsa a matsayin matarsa......a jininki da nashi kawai nakejin zaku fahimci juna koda baku magantu wa junanku ba....." Maganan tata ta sake kaiwa qarshe da wani irin taushi. "Ki zauna dashi..." "Ki kula dashi......Allah ya tsareku". "To nanay.....na gode" Ta fadi da wani harshe data fara koyon ladabin magana dashi. Wani harshe da yake mata dadi matuqa....wani yanayi da ita kanta idan tayi magana da mutane dashi yake burgeta. Idanunta ta lumshe sosai tana relaxing bayanta jikin makarin kujera. Taja iska sosai cikin hunhunta sannan ta fiddata a hankali. Tunaninta gaba daya yana komawa kan nanay ne. Tana jin ta aza mata wani nauyi me girma amma kuma sai takejin kamar dolenta ne. Ta kula dashi.....ta kula dashi.....idan baida lafiya yana koma mata kamar qanqanin yaro ne.....ta yaya?,ta ina zata fara da wannan aikin me girma da nanay ta aza mata?. "Zaki iya akhnan.....zaki iya......darajarki....martabarki da mutuncinki a idanun nanay....... Zaki iya akhnan......ki tuna,ya sadaukar......da sadaukar da yawa a kanki......ki tuna akhnan,ya baki kariya ya kula da ciwonki mabanbantan lokuta.....a lokutan da bakisan daraja da girman kulawar ba" Maganar data fara mata yawo kenan a kanta,ta bata wani qwarin gwiwa,ta kuma sanyata bude idanunta a hankali ta maida dubanta kan wayarta. Number birra ta laluba,bugu daya kamar kullum birran ta daga. "Kada ku damu da rashin dawowata birra....." Saita gaza qarasa mata tana jin kamar yayi nauyi ta gaya musu tana gurin sheikh haisam.... "Karki damu uwar gijiyata,nanay ta yimin bayani,yanzun haka ina kan hada miki kayayyakin da zaki iya buqata zuwa sassan" "Na gode" Kawai tace da birran tana yanke kiran. Iska ta furzar daga bakinta,qwaqwalwarta tana mata bita da tilawar wasu daga cikin qa'idojin masarautar data karanta. Zata zama daga ita sai haisam cikin sashen kenan iya adadin kwanakin,baqi hadimai ko bayi sai idan su suka lamunce musu shigowa. Duk wani guri da yayi kusa da falukan dake kewaye da dakunan baccin sashen ba wanda yake da ikon zuwa sai bisa sahalewarsu. Zuciyarta tadan buga kadan,ta ware tafukan hannunta tana kalla kamar wadda take neman shawara daga gurin wani. Koda ta kira shehnaz a yanzun tana jin ita da shehnaz din suna rayuwa ne a mabanbantan duniyoyi. Babu lallai ta fahimci komai daga cikin abinda zata gaya mata. Falaak ce....kuma tana jin nauyin magana data shafi haisam da ita. Ita din gaba take da ita,kamar yadda dukkaninsu haisam din yake gaba dasu. Qarar wayartata shine ya sake dawo mata da tunaninta daga inda ya tafi,birra ce,ta daga kiran tana sakawa a kunnenta ba tare data ce komai ba. "An kawo komai da komai ranki ya dade" "Na gode birra" Ta fada a nutse. Bin wayar da kallo birran tayi,a yanzun data koyi godiya abun mamaki yake baiwa birran,mamakin me yake sauya dabi'arta ne sannu a hankali a hankali?. *zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 08187255862 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 08187255862 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 69* Kayan jikinta ta kalla,suna da dan nauyi kadan,bata iya zama da kaya masu nauyi harta wuni dasu,me ya kamata tayi yanzu?,ta ina zata fara abinda ya dace?. Miqewa tayi tsam ta soma takawa zuwa hanyar fita ko zata samu kayan da birran tace an shigo dasu,saidai tana bude qofar ta tsinci suitcase dinta tsaye a qofar dakin. Ta danji mamaki kadan,don tasan ba lallai birra ta iso gurin,to waye ya iso da ita?. Bata tsawaita tunaninta ba ta jawota zuwa dakin da kanta,wani abu da cikin rayuwarta ba zata iya tuna sau nawa kwata kwata ta taba yinsa ba. Ta kwantar da ita tana budeta saqo ya fado cikin wayarta. Hannu ta sanya ta dauki wayar,ganin sunan nanay ya sanyata komawa ta zauna sosai tana kallon wayar. A nutse take bin rubutun,wani irin tsararren menu ne nanay ta shirya mata. Yadda zata kula dashi step by step,kowanne minti zuwa awa daga safiya zuwa dare. Koda ta gama karantawa murmushinne ya sake subuce mata "Ya Allah,na gode daka ceceni" Ta motsa labbanta a hankali tana furtawa. Sosai taji dadi.....taji dadin menu din,kamar tasan abinda take saqawa kenan a ranta,yaya zatayi?. Menu din ya zame mata kamar wani d'an jagora a sanda take cikin tsananin duhu. Ajiye wayar tayi ta miqe tana sake bude jakar. Ga mamakinta atamfofi a ciki dinkakku,lafiyayyun super Holland vlisco masu asalin kyau da taushi,marasa nauyi wadanda zasu baka daman sakewa cikin dinkunansu. Mamaki kadan ya kamata,yaushe yanayin tsarin jaka da suturarta ya sauya?. Duk da bata da masaniyar komai akan suturarta amma wannan sauyin yadan bata mamaki. Hakanan ta cire doguwar riga a ciki,wadda aka mata wani budadden dinki daga qasa,ya bude sosai,ya kuma zauna das a qirjinta,ya fitar da dogon wuyanta da kafadunta dake tsaye kyam wadanda suka dace da qirar jikinta. Tsaiwa tayi tana kallon kanta sosai,Dinkin ya taimaka wajen fitar da shape din qugunta daya baje sosai tare da budewar da rigar tayi ta qasanta. Cikin ranta karo na farko da taji atmfa ta shiga ranta,ta kwanta mata a rai. Tayi qoqarin ta daura dankwali amma ta kasa,duka hannuwa suka gaji,sai kawai ta wurgar dashi a nan,ta matsa ta dauki wani mayafi data gani cikin kayan ta yafa saman sassalkar sumarta. Takawa tayi a nutse tana fita daga dakin,sannu a hankali sai hankalinta ya rarrabu wajen neman qofar fita. Kamar wadda aka juyarwa da kai,kaman bada qafanta ta qaraso dakin ba,kaman bayan shigowarta an canza tsarin ginin gurin,saita kasa tantance qofar fita,dole ta dinga bi hanya bayan hanya tana dubawa. Qofa ta qarshe taga tayi mata kama da qofar data shigo din a dazun,tadan lumshe idonta ta aza hannunta akan handle din tana addu'ar Allah yasa ta dace can dince. Yadda ta soma tura qofar cikin nutsuwa haka yake daga kanshi cikin nutsuwa yana sauke nakakkun idanunsa dinnan a kanta gaba dayanta. Zaune yake kan wata irin sofa da zata bashi daman hutawa dama miqewa qafafuwansa sosai. Yana jingine da wani tattausan massage pillow a gadon bayansa yana amsa wayar da tsabar nutsuwa irin tasa bakajin abinda yake fadi,sai wadannan labban nasa masu sulbi dake motsawa a nutse. A hankali ya soma tafiyar da idanunsa yana sauke mata wani irin kallo,tun daga saman kanta da mayafin data yafa ya zame zuwa rabin kanta saboda haduwa da yayi da sassalkan gashin kanta,har zuwa zara zaran yatsun qafarta da suke nutse cikin tattausan carpet din dake malale a parlor din. Wannan kallon yaji bai masa ba......sam bai masa ba,bai isheshi ba bai gamsu ba,sai ya sake maida idanun nasa daga qafarsa yana aikensu zuwa ga jikinta a karo na biyu. Tsaiwa ta farko ya dakata daidai qugunta dake juyawa a hankali sakamakon takowa da takeyi zuwa ciki,sannan qwayar idanun nasa suka sake tsaida birki akan cikakkun qirjinta da suka cika rigar jikinta. "Hutun sati biyu suka bayar.....sunce kayi haquri ka karba a haka,akwai sauran qananun case......" Maganan da omar yake fadi masa kenan ta cikin wayar da yaji ta fara nisa da kunnuwansa ainun,saboda zare wayar da yayi daga kunnen nasa ya ajiyeta kawai a gefansa ba tare daya damu da kasheta ba. "Subhanallazi khaaliqunaa" Ya fada can qasan maqoshinsa adam apples dinsa yana kai kawo tsakanin maqogoransa daga farko zuwa qarshe. A hankali taji kaman qafafunta suna lanqwashewa......wannan nauyin dake cike da narkakkun qwayar idanunsa yana sauka a kowacce gaba ta jikinta. Wani irin kallo da ta jishi a yau har cikin jininta.....wani irin kallo da takejin kamar sai ya huda fatarta sannna ya huda tsokarta,ya kuma huda qashinta sannan yakai ga bargonta bayan ya tsinke kowacce jijiya ta jikinta. Wani zuzzurfan kallo da bai taba yi mata irinsa ba.....wani irin kallo da a yau karon farko ta jishi sama da kowanne kallo daya taba yi mata a rayuwarsa. Sallama takeso tayi masa amma ta kasa......duk yadda taso motsa labbanta tayi sallamar amma abun ya gagareta,saidai ga tarin mamakinta sai taga ya motsa labbansa yana lumshe wadannan narkakkun idanun nasa yana furta. "Wa'alaikumussalam warahmatullah" Abinda yadan qara mata rudani akan wanda take ciki. Itace ta samu nasarar yin sallamar ba tare data lura ba?,ko kuma shine kunnuwansa sukaji masa haka?. Ta qarfafi kanta da dukkan iyawarta,ta samu takai kanta saman daya daga cikin sofas din dake daura da tasa ta zauna. Qasa tayi da kanta kada,har yanzu tana jin nauyin idanunsa dake kowanne sashe na jikinta. "Sannu......ya jikin?" Ta fada da hausa saboda bataso ya amsa mata da French ya qarasa kassara mata zuciya a daidai wannan yanayin da take qoqarin daidaita kanta da qoqarinta. "Alhamdulillah" Ya fada kaman wanda yake tsoron kada aji sautinsa,yana maida jikinsa ya jinginar ga massage pillow din still idanunsa a kanta,baiyi kuskuren janyewa ko sau daya ba. "Akwai magunguna inji nanay a cikin gurincan......amma kafin sannan me zakasha?.....coffee ko black tea?" Ta fadi tana daga blue eyes dinta da wani irin sanyi tana zubesu a fuskarsa. Ji yayi a sannan kamar yana nutsewa cikin ruwan qanqara......wani irin abu me sanyi yana ratsashi daga cikin idanunta kai tsaye zuwa cikin nasa idanun dama gangar jikinsa gaba daya. "What a beautiful eyes" Ya furta can qasan maqoshinsa,labbansa kadai suna motsawa a hankali ba tare da sautin ya fita ba. Duk wata laka ta jikinsa ta gama zare masa ita,bayajin bakinsa zai iya cewa komai da ita,sai kawai ya daga mata kai a hankali. Wannan kallon nasa kasheta kawai yakeyi......wadannan idanun nasa,har yanzu bata tsinci wani abu dake kassarata ba.....wani abu dake mata illa kaf rayuwarta ba irin yadda idanunshi yake da tasiri a kanta ba. Ta motsa tana miqewa a hankali,still ya sakejin bazai iya raba idanunshi da kallonta ba. Binta yayi da kallo da dukka idanuwanshi......irin kallon nan nakai tsaye yana kallon yadda take dagawa da sauke Qafafunta a hankali,yana kallon yadda qugunta ke juyawa kamar da gayya takeyin hakan dashi.....yana kallon yadda iska ke kada mayafinta hade da gashinta daya fito ta qasan mayafin. Har ga Allah kallon ya mata nauyi.....har ga Allah takejin yadda idanunsa ke keta kowanne tsaro na jikinta,da wannan qarfin halin da wannan qarfin gwiwar tabi direction din dake nuna mata inda kitchen din gidan yake takai kanta kitchen din da qyar. Daidai lokacin da take cikin kitchen din,take binsa da kallo kusurwa kusurwa. Karo na farko a rayuwarta data samu daman taka cikin kitchen din,bama kitchen din ba,karon farko data kusanci cikin aninihin ginin nasa kenan. Tana ji a ranta zata riqe amanar haisam kamar yadda nanay ta buqata.....zata riqe amana kamar yadda tace a gabanta.....amma hakan ba yana nufin zata kasa ko zataqiyin yaqin da zata samu nata gurbin da muhallin a zuciyarsa ba. Hakan kuma ba yana nufin zata kasa yaqarta ta hanyoyin da tasan zata tsira da nata kusancin da soyayyar ba. Tsaiwa tayi a hankali tana jingina da qofar kitchen din,tana jin adadin bugun zuciyarta,saita maida idanunta ta lumshe tana qoqarin saita bugun zuciyartata. A baya ta dauka ita din jaruma ce,a baya idan akace mata iri ko shigen haka zai faru da ita game da wani d'a namiji.....ya sakata fargaba.....ya ninka bugun zuciyarta to zata qaryata hakan......amma cikin lokaci qanqani ya zama namiji na farko daya fara birkita lissafin qwaqwalwarta dana rayuwarta gaba daya. (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) "Me yake kallo?.....me yake kallo haka tattare dani?" Ta yiwa kanta da kanta tambayar murmushi yana qwace mata tana kuma bude idanunta a hankali. Cikin idanun samee nata idanun suka sauka,saamee din da tayi tsaye tana qarewa akhnan din kallo wani kibiyar kishi yana hudata "Haka take da kyau?,haka take dama?" Ta maimaitawa kanta tambayar har taji kaman zata zauce cikin qasa da minti uku. Wannan shine karo na farko data ganta kusa da kusa haka,ba shigar nan me nauyi me ado da take tunanin ita ke qara kwarzantata da qara mata kyau,ashe shigar ba abinda take mata sai sake boye kyanta. Haka kawai taji yarinyar batayi mata ba. Halittarta ce bata qaunar SHISHSHIGI sam,idan zata soka zata soka kawai.....idan baka mata ba baka mata ba. Batason a dinga shiga al'amuranta tun asalinta,wannan ya sanya tashin farko aka samu wani irin clashing me girman gaske tsakaninta da saamee. "Barka da warhaka" Saamee din ta fadi,saidai tana cire kusan fiye da rabin irin girman daya kamata a al'adance ta bata cikin gaisuwar. Minti kusan guda cikakke,minti gudan da saamee ta cire tsammani ta fidda rai akhnan din zata amsa mata,bayan minti gudan sannan muryarta ta motsa da "Barka" Ta fadi tana takawa da wannan tafiyartata da saamee ta tsana. Wannan tafiyar da take sawa saamee din taji ita qasqantacciya ce.....wannan tafiyar da saamee ke jinta kamar cikin tsakiyar ranta. "Me kike da buqata?" Ta furta tana d'an duban akhnan din da taga tana wucewa kai tsaye zuwa kitchen island din dake tsaftace ba komai a samanshi. Bata amsawa saamee din ba,don hankalinta ma bawai yana kanta bane kwata kwata. Tunaninta da hankalinta yanzun ya tafi ne akan recipe na black tea da nanay ta aika mata cikin menu dinnan. Kayan hadin da komai daya kamata ta saka. Zata iya?,zai shawu?,a karon farko ita akhnan zata dafa wani abu a duniya?. Yadda bata amsa mata ba,haka saamee bata sake cewa komai ba,bata kuma fita daga kitchen din ba. Taja baya ta tsaya tana qarewa akhnan kallo qasa qasa. Yau wataqila ta zama ranar farinciki ta farko a gurinta. Ranar da akhnan din zata gaza dafa abinda ya shigo da ita kitchen din,wanda koma meye ta tabbatar haisam dinne zaiyi amfani dashi. Ta fahimci hakanne saboda kusan salo da pattern don nanay kenan. Sarrafa komai da motii zaici ko yasha da hannunta muddin tana da lafiya. Ta sani.....ba abu bane boyayye,akhnan din ta fito daga gidan sarautar da ita daya ce suka mallaka......ta kasance SHALELE ba'a masarauta kadai ba......har a dukka qasar agadez gaba daya. Tana qarqashin kulawa da tarin hadimai....to mene zata iya?,me zata iyayi saidai komai ayi mata. Daga wucewarta yaji parlor din ya masa shuru.....daga wucewarta sai yaji kamar ta wuce da komai....komai kamar ya tsaya kaman yadda wayarsa da omar ta katse ba tare daya sani ba. Baiyi wani tunani na biyu ba kawai ya miqe a hankali,ya zura tattausan slipper din daya dace da yanayin shigarsa ya soma takawa a hankali kanshi tsaye yana nufar kitchen din. *zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 08187255862 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 08187255862 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 70* Ta gama duba duka kayan hadin,ta kumayi qoqari sosai wajen fidda komai ta ajjiye saman mulmulallen bar counter dake kitchen din,wadda aka zagayeta da wasu irin kyawawan kujeru masu tsaho. Sake komawa tayi tana duba bangaren electric din dake ajiye guri guri cikin tsari a kitchen din,duk wani nau'ikan kayan wuta kala kala,a nutse ta zabi coffee maker dan madaidaici daya,ta dawo dashi saman bar counter din ta ajiye. Kayan hadin tea din take dubawa da daya da daya tana zubawa,kai zakace batasan da tsaiwar saamee cikin kitchen din ba. Koda motsinta bazai nuna maka tasan da tsaiwarta ba ballantana aikinta. A nutse ya tura qofar kitchen din da sallama a bakinsa cikin sautin nan nasa. Husky voice dinsa me wani irin zurfi da sautin amo me tsayawa a rai da zuciya. Idanunshi a kanta yana mata wani duba me dauke da mamaki,ta masa wani irin kyau da tsaiwarta a kitchen din,sai ya ganta wata mace ta daban. Ba wannan akhnan din ba yake kalla ba.....ba wannan biftu din ba.....ba wannan khadeejan ba princess of agadez ba. Wata matar gida....responsible matar gida. Da iya tambayarsa kawai da tayi me zaisha din?,ta gama kwance masa tunani.....da iya tambayar data masa kadai a dazun ta goge masa tunani.....ballantana yanzu da yazo ya sameta a tsaye da nufin zata dafa abinda zata bashi da hannunta?. "Ya salam....." Ya fada a hankali,mamaki yana sake kwance masa kai. "Barka da warhaka obbo......fatan ka fito lafiya" Saamee ta fadi da wani iri narkakken ladabi yana lanqwashe kanta. "Barka kade" Ya amsa mata idanunshi da zuciyarsa gaba daya suna kan akhnan dake auna adadin kayan hadin tana zubawa cikin mini coffee maker din. "Ya jikin?,Allah ya qara lafiya me dorewa". Ta fada tana satar kallonsa. " Ameen" Ya amsa mata,daidai sanda idanunta sukayi kyakkyawan gani. Hankalinsa da gangar jikinsa dukka akhnan suke nufa. Wani abu me nauyi ya danne mata zuciyarta. Bataji zata iya bar musu kitchen din,bata jin zata iya basu wannan space din,duk da adoka da qa'ida barin kitchen din ya zama wajibi a kanta. Taji shigowarsa......sallamarsa da takowarsa.....amma bata daga idanu sam ta kalleshi ba,saita zabi ci gaba da abinda takeyi. Wani bala'in burgeshi tayi.....wani bala'in tafiya tayi dashi. Wannan jan ajin.....wannan basarwar,wannan dauke kan data sake masa sanda yake jan daya daga cikin kujerun bar din ya zauna idanunsa zube a kanta. Baice mata komai ba kaman yadda batace masa ba,sai wani irin kallo daya kafeta dashi tamkar an bashi gadinta da aikin lissafa duk wani motsi nata. Taji idanunsa a kanta,amma still bata dago ba,kallonshi yakeso tayi....koda sau daya ne da wannan blue eyes din nasa,amma akwai alamu gilmawar wani irin izza a idanu da fuskarta da yake hange. Ya fahimci da gaske ba zata kalleshi ba,sai ya miqa zara zaran yatunsa ya zare cokalin da take saka amount na hadin tea din yaci gaba da zubawa shima ba tare da yace komai ba. Hakan baisa ta kalleshi ba,taci gaba da tsaiwa kawai tana harde hannayenta a qirjinta. Kawai takejin batason wanzuwar yarinyar a kitchen din. Haka kawai takejin zamanta a kitchen din bai mata ba. To amma ba zata bata kalmomin bakinta ba ko sau daya a kanta ba. Tunda tazo Ethiopia ko sau daya ba wani wanda takejin bai mata ba......amma akan saamee taji wannan,bawai tana da wani babban dalili bane,don bata da lokacin saka hankali da idanunta akan kowa sai akan abinda ya shafeta tun asalinta SHISHSHIGI shine kawai abinda bataso bata qauna. "Saamee" Abinda ya fadi kenan idanunsa akan coffee maker din da yake duba adadin kayan daya zuba. Ba tare daya qara kowacce kalma ba saamee din ta soma takawa tana fita daga kitchen din. Zuciyarta kamar zata fashe.....fadin qirjinta tana jin ya yiwa zuciyarta kadan,wani abu ya dunqule mata ya fidda wani zazzafan hawaye daya sauka saman kuncinta. Kunnata yayi ya saitata,sannan a hankali yaja kujerarsa baya yana zube idanunsa akan Akhnan. Still miskilar tasa ba abinda ya sauya,kamar tasan me yake buri?,sai kawai ya miqe a hankali yana aza hannunsa saman sassalkar sumarsa da duka yau take a hargitse yana sake hargitsata hade da wani yanayi da yaji yana yamutsa kwanyarsa gami da saukar masa da wani irin tashin tsigar jiki. Ganinta yake son yayi in full details bada wannan mayafin ba.....so yake ya ganta gayarta,don haka ya soma takawa a tausashe,ya kuma mamayeta ba tare data ankara ba,saiji tayi ya debe.mayafin kanta gaba daya ya duqunquneshi cikin hannunsa. Sanda ta juyo yana dunqule mayafin ne,ya kuma zuba mata ido yana ganin yadda sumarta ke warwarewa daga dan qulletan da tayi da sirirn band. "Ma sha Allah" Ya fada can qasan ranshi yana hadiye wani yawu. Yadda sumar ke sauka tana bajewa zaman bayanta har dab da mazaunanta ya sake harba wani abu me qarfi gaske zuwa ga sassan jikinsa. Ta zube masa blue eyes dinnan da yaga tsoro qarara a cikinsu. Taku daya yayi ya isa gareta,ya kuma.jawota cikin jikinsa,wannan karon bai jira komai ba ya mata wani kyakkyawar runguma data amsa sunanta cikin jikinsa. Wannan karon.....bada gangar jiki kawai ya rungumeta ba,wannan karon da dukka zuciyarsa ta dinga ji kaman ya rungumeta,ya narke mata sosai cikin jikinta,ta motsa kadan amma sautinsa ya sauke mata komai. "Jinyata nanay tace kiyi please,ba haka nanay takeyimin ba....idan bani da lafiya na kwanta akan cinyarta.....bata cewa na tashi......kada kici amanar da nanay ta baki mana" Ya fada yana sake shigewa cikin jikinta kamar dukka burin rayuwarsa dama maslahar rayuwar tasa ta ta'allaqa da dogon wuyanta ne. Tana da saurin amincewa da maganar mutumin duk da ta bawa fili har ya shiga rayuwarta,don haka bata ji cewa maganansa ba haka bane,saita daina yunqurin zamewar,ta tsaya sosai kaman yadda yakeso,wannan ya bashi daman sake laqumeta cikin faffadan qirjinsa yana sansanar qamshinta sosai kamar zai zuqe duk wani qamshi da yayi saura a jikinta. Cikin mintuna qalilan yaji ya fara birkicewa. Itama birkicewar ta fara yi,don ba qaramin dafi yake saukar mata ba daga zazzafan numfashin da yake saukewa wuyanta,sannan taji ya fara sauya akalar yana kawo hancinsa saman qirjinsa kaman yana son cusa kansa tsakanin halittun qirjin nasa. Fuskarsa ya zare a hankali sanda coffee machine din ya kashe kansa da kansa bayan yakai inda ya kamata yakai. Ta dauka zai zare jikinsa ne.....amma ga mamakinta sai kawai taji ya dagata cak ya dorata saman kitchen island din. Bar chair din ya jawo dab da ginin da take kai a zafafe sannan ya zauna akai,ya raba cinyoyinsa tsakanin nata,nata qafafun suka kasance tsakiyar nasa. A yau yana jin duk wani qarya da yakewa kansa tana warwarewa.....kafiya da taurin kansa yaji gaba ana kwanceshi daya bayan daya. Yasa hannunsa,ya kamo zara zaran yatsunta ya cusa tsakiyar nasa ya matsesu gam,saidai a tausashe yadda ba zataji zafi ba. Ya zuba musu idanu yana kallonsu kafin ya maida dubansa ga fuskarta sannan qirjinta dake wani irin bugawa. "Bugawar da zuciyarki takeyi a kullum tana wuce kima" Ya furta softly yana lumshe idanunsa kamar wanda ya tashi daga baccin da bai isheshi ba. Qoqarin daidaita numfashinta da bugun zuciyarta ta soma yi,saidai ya hanata wannan damar ,yama sake rikita mata lissafinta gaba daya sanda yace da ita. "Sau nawa zuciyarki zata gaya miki sona kike kafin ki amince da abinda yake gaya mikin?" Saura kadan,saura qiris numfashinta ya qwace mata,saura kadan ta rasa fitar numfashinta na daqiqa ta samu ta riqeshi da qyar ta hanyar zaro idanunta waje......amma wadannan tsimammun idanun nasa.....wadannan idanun nasa masu cike fal da dafi da maganad'isu suka hanata masa qarya,illa furta kalmar. "Ni?" Da tayi adan birkice. Duk da abinda yakeji cikin jikinsa amma hakan bai hanashi sakin wani siririn murmurshi ba bayan ya lumshe idonsa ya kuma.budesu yana gyada kansa. "Yes.....ko kin bani dama na fiddo gaskiyar hakan?". Wani sabon kallon daya watsa mata ya sanya ta fara jin kamar narkewa takeyi tana bin jikin island din,sai kawai ta yanke ture yatunsa a gigice tana fadin. "Tea dinka ya zama ready" "I know" Ya amsa mata kai tsaye yana sake hanata damar sauka daga kan island din kamar yadda tayi niyya da farko. Yana sake mamayeta da hannuwansa. Ta bayan mazaunanta ya zagaya da hannunsa,ya kuma soke yatsunsa cikin na juna,ya mata qawanyar da babu damar ta motsa,gwiwoyinta suna tokare da qirjinsa,sai kawai ya sanya kafadunsa ya raba tsakanin qafafunta ya shige ciki yana dora kansa saman tattausar cinyarta. Gigicewa tayi gaba daya,ta dora duka hannunayenta saman kansa da niyyar ture kansa,saida dogayen yatsunta tuni suka samu daman nutsewa cikin tattausan gashinsa. Wani irin abu yaji yana ratsashi,ya lumshe idanu yana sauke wata ajiya zuciya. Kaman susa take masa cikin kan kasa yaji,wani abu me dadi yana ratsa tsakiyar kansa nasa har cikin kwanyarsa. "Karki janye......don Allah....." Ya fadi a hankali sanda take zare yatsunta ganin yadda ture kan nasa bai tsinana mata komai ba. "Pleaaseeeeee" Ya sake fada da wata irin raunanniyar murya. "Don Allah.....amana nanay ta baki.....na tabbatar nanay tace ki kula dani" Ya sake fadi yana qara matse cinyoyinta zuwa mazaunanta tare da nutsa kansa sosai cikin cinyarta kamar zai narke ya zama daya da fatar jikinta. (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) Yadda yayi maganan.....yadda ya fada din sai ya kasheta jiki gaba daya,saita samu kanta da tura yatsun nata kamar yadda ya buqata a hankali da wani irin yanayi da batasan zai haifar masa da komai ba. "Biftuuu" Ya kirata a nutse yana karya shurun daya ratsa tsakaninsu,idanunsa suna lumshewa da budewa gami da sake jirkicewa daga launin kalarsu. "Na'am" Ta fada a hankali tana zare hannuwanta saboda wani irin bugawa da taji zuciyarta tana yi daga cikin qirjinsa dake kwance saman cinyoyinta. "Akhnaaan" Ya sake kiranta,wannan karon kiran daya mata har yafi ka dazun,a daburce tace. "Shayinka ya huce" "Na sani" Ya fada da birkitattun idanunsa daya daga yan kallonta. Kallon ya mata nauyi,kashe mata jiki yake sosai....kwarjininsa narkata yakeyi,saita kau da kanta gefe tana jin kowacce gaba ta jikinta tana amsawa. "Zakasha magani......ka bari na dauko maka kasha.....don Allah" Ta qarashe roqo,don neman inda zata kufce takeyi. Kamar bazai janye ba,kamar ba zaice komai ba,sai taji yana zare hannuwansa a hankali daga jikinta yana binta da wani sassanyan kallo. Rawa hannunta yake sosai sanda take zuba masa tea din a cup. Nisan tunanin da tayi ya sanya cup din ya kusa cika bata sani ba. Gigicewa tayi,saboda wani abune da bata saba ba. Hannunta na rawa takai hannunta kan makashin,wallahi takai ga dannawa taga dogon yatsansa me wasu irin fararen farce tamkar baisan wani abu da ake kira da dauda ba ballantana qura. Janye hannunta tayi,saita daga idanunta suna hada ido dashi. Girarsa daya ya dage mata,ta kauda kanta da sauri tana neman hanyar da zata zame,saboda ya tazarar dake tsakaninsu duka duka bai wuce taku hudu ba tsakani. Daga nan tana iya jin saukar sassanyan numfashinsa. Daga nan tana iya jin qamshin jarababben turarensa da ya manne mata jikin kayanta gaba daya kaman yadda ya game jikinsu gaba daya "Ki bani" Ya furta a shagwabe da wani irin laushi yana qare mata kallo tamkar Allah ya aikoshi. Tadan kalleshi kadan a sace tana mamaki. Gashi ga tea din,asalima shine ya kashe maker din amma ya dauka baze iya ba. "Kiyi haquri.......bani da lafiya,kula dani akace kiyi sosai,haka nanay ke kula dani idan bani da lafiya. Nayi kuka akan cinyarta....nayi bacci duka bata hanani" Ya fadi da wani irin laushi. Yadda yake maganan sai taga ya koma mata yaro qarami,irin qanqanin yaron nan da bai wuce shekara goma ba. Kasa jurewa tayi,sai data sake satar kallonsa sannan ta kauda kai da sauri. "Baki yarda ba ko?" Ya fada sanda take miqa masa coffee din,sai ya hada da yatsunta ya riqe cikin nasa yana kasheta da narkakkun idanunsa. Yadda yake kasheta gaba daya tana jin kamar zuciyarta zata narke ta fito daga qirjinta,sai taji me yayi saura,narke masa nata idanun tayi kamar me neman tallafi. Wani abu ya damqi zuciyarsa da wani matsa da sai daya lumshe idanunsa sannan ya budesu "Zaki yarda......." ".......wataran" Ya fadi kalmomi biyun a rarrabe yana sakar mata hannun a hankali. Zama yayi saman kujerar bar din yana sipping coffee din a hankali. Yayi dadi....dadin da baisan me yasa yayishi ba. Hannunsa ne ko hannunta,ko qare mata kallon da yakeyi sanda take kai kawo tana duba freezers din kitchen din bayan ya hanata dankwalinta qememe. A duk sanda zatayi taku daya sai yaji gaba daya duniyarsa ta girgiza,ya zame mug din yana ajiyeshi sanda yaji haqurinsa yana qarewa. "Halal dina ce.....lada Allah zai bani" Ya fadawa kansa da kansa yana jin yadda tafin hannunsa dana qafarsa suna daukan wani irin dumi. Agogo ya kalla yana duba lokacin sallah,a hankali ya zame dubansa yana fadin "Lokacin sallah yayi" Muryarsa a shaqe tana fita da qyar. *zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 08187255862 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 08187255862 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 71* __________________________ *_Amintaccen gurin siyayya_* *_ingantattun kaya akan ingantaccen farashin da ba irinsa a kasuwa_* *_BONONZA DA PROMO akai akai_* *dukka sai a HUGUMA CLOSET* *Duniyar kayan yara,mata,maza,dukka* *shaddodi,atamfofi,laces,abayas,jakankuna,takalma,agogo,sarqoqi,English wears,night wears,under wears,da duk wani nau'in sutura babba da qarami* *_Karki yadda ayi babu ke.....leqa kiga yadda closet din HUGUMA kullum ke cike da kaya akan farashi me kama da KYAUTA_* *_YAN SARI....YAN REPOSTING.....DA SARAKAN ADO MASU SIYA DON KANSU....DUKKA INA MUKU MARABA_*🤝🤝🤝🤝 https://chat.whatsapp.com/FrqgC0YmUWP4FPmUzYuLJX __________________________ Kallonsa tayi sannan tayi qasa da kanta,batasan yadda zata gaya masa ba,batasan yadda zatace masa bata sallah ba. Kunya da nauyi takeji,idan tana period dinta ba wanda ya sani,batasan ta inda zata fara masa bayani ba sam. Baiko motsa ba,shi da yace lokacin sallah yayi amma yana tsaye hannayensa harde a qirjinsa yana qare mata kallo. Alamar jiranta yakeyi kenan?. Kamar yasan tunanin da take ya motsa labbansa a hankali muryarsa can qasa. "Bani da lafiya....kuma kin sani,amma kin barni a tsaye ina jiranki,muje muyi sallah" Ya fada idanunsa suna lumshe kansu gami da budewa lokaci guda. Dole ta juya a hankali ta fara takawa,ya bita da idanu a nutse yana jin kamar tana tafiya da wani sashe na zuciyarsa. Kamar me gadi da ubangidansa haka yake biye da ita,yana sauke kowacce qafarsa a inda ta dauke tata. Takunta......wani irin yanayine a cikinsa me tafiyar da hankali,wani irin taku da yakeji kamar ya banbanta da sauran dukka wani taku daya sani. Kowanne sashe na jikinta yana motsawa a sanda ta daga qafarta ta kuma sauke da wani irin yanayi me janye hankali. "Ya salam" Ya fada idanunsa suna sake lumshe kansu gami da budewa bayan da zuciyarsa ta d'arsa masa. "Maza nawa sukaga wannan takun nata?,maza nawa suka kalleta?,qasashen duniya nawa taje suka kalli wannan jikin?". " Ba haka bane" Zuciyarsa ta sake fadi masa bayan data shiga masa tariyar halinta. Adadin mazan da ta hanawa damar kallonta kadai......adadin mutum nawa ma suka samu damar ganinta ido da ido,sassanyar ajiyar zuciya ta subuce masa daidai sanda idanunsa suka sauka akan saamee. Da wani irin sauri ta dauke idanunta daga kansu zuciyarta na wani irin bugawa. Bugun da takejin kamar zai hadu ya tarwatse da zuciyartata gaba daya. Yadda suka jero,yadda yake biye da ita kamar salon karin maganar nan da ake kira da raqumi da akala. Fes idanunta sukaga yadda yake qarewa komai nata kallo ta baya. Wani abu ya tsaya mata a wuyanta ta dinga jin kamar zatayi amai. "Barka da fitowa" Kalmar ta fadeta ne saboda taja hankalinsa ko yaya,amma haka kawai yaji Kalmar tazo tayi masa karen tsaye. A yadda yakejinsa dinnan,bayason kusanci daga kowa sai daga gareta,baya buqatar motsin kowa a duniyarsa sai nata. Baya marmarin numfashin kowa kusa dashi sai nata sassanyan numfashinnan da yake fita da wata irin kalar nutsuwa. Kai kawai ya daga a nutse yana ci gaba da binta a baya. Ta danji mamaki kadan sanda taga shima ya tura qofar dakin data shiga din ya shiga. Ta waiwayo tana dubansa da shagwababbun idanun nan nata. A zahiri zakace shagwaba takeji......amma a bad'ini shi yake narka mata zuciya gaba daya,wani irin MAHAUKACIYAR SOYAYYA takeji tana huda fatarta tana ratsawa zuwa ga jinin da zuciyarta ke aikewa zuwa kowanne sashe na jikinta don samun rayuwa yadda ya dace. "Ki fara yin alwalar" Ya fada a mugun kasalance yana jin yadda mararsa ke sake daurewa kaman bazai iya sake taka qafarsa ba daga gurin,saidai duk da hakan hannun rigarsa yake nannadewa zuwa gwiwar hannunsa. "Ko mu shiga tare?" Ya fadi da wani yanayi na kaman neman izini yana narka idanunsa cikin nata. Idanun nata ta dauke,harshenta yayi nauyi,period ta gama dazun da safe,tana kuma sanya ran ganin tsarki daga kowanne lokaci daga yanzu,saidai batasan sanda zatayi wankan ba bare tayi sallah,don bata sake dubawa ba bare ta tabbatar da jufuf ko qassatul baidaah,wanda ita nata qassatul baidaah dinne(kamar yadda yazo a musulunci alamun tsarki guda biyu ne,yana da kyau kowacce mace ta kula da wannan lokaciin,a wannan yanayin wasu suna barin sallolinsu da yawa,akwai ramuwar sallah game jinin al'ada,mata da yawa kuma basu sani ba,sai a kula da kyau). "Biftuuu" Ya kira sunanta da wani accent daya sanya taji dukka wata tsiga ta jikinta ta miqe,kafin tace komai kuma ta tsinceshi dab da ita. Zullewa taso tayi saboda tana jin kamar cikin wucewar kowacce daqiqa kasheta yakeyi........kasheta yakeyi da idanunsan nan.....sautin muryarsa......qamshin turarensa......da wani irin kusanci da kaf duniyarta bata taba tunanin akwaishi ba. Nuna mata banbacin dake tsakaninsu yayi,da wani irin zafin nama ya riqo hannunta cikin nasa sannan ya jawota gaba daya,sai gata tayi kyakkyawan masauki cikin qirjinsa. Wani irin shuru me dauke da wani irin yanayi ya gilma a tsakaninsu. Jikinta takeson zamewa saboda wani irin nannauyan yanayi da yake bata,wani yanayi daya aza mata wani irin tsoro saboda yadda takejin jikinsa sosai cikin nata,amma yadda taji bugun zuciyarsa da numfashinsa suna fita sai tsoro ya kamata. Ta daga idanunta da sauri tana dubansa,sai ta sake daburcewa ganin yadda wadanan manyan fararen idanun nasa suka sauya launi sannan suka rusuna girmansu yana raguwa sosai. "Jikin naka ne?" Ta tambayeshi tana dan rudewa,rudewar data nuna har cikin wadannan blue eyes din nata masu daukan hankali. "Bani da lafiya biftuuu......bani da lafiya" Ya fada muryarsa tana rarrabewa saboda yadda yakejin numfashinsa yana neman masa kadan. Qoqarin zamewa tayi tana fadin. "Sannu.....bari na dauko maganin da nanay tace....." Maidata jikinsa yayi yana fadin. "Wannan maganin ba?.....wannan maganin bazaiyimin komai ba biftuu" Yayi maganar kamar qaramin yaron daya rasa uwa a sanda yake tsananin buqatarta yana kwantar da kansa saman kafadarta. "Sai wanne?,saina yiwa nanay magana a kawo" "Kece......kece maganin akhnaann!" Ya fadi da wani irin harshe muryarsa tana komawa can qasan maqoshinsa yana sake matseta a jikinsa kamar zai ballata. Wani irin shuru tayi zuciyarta na bugawa da matsanancin guda da taji kamar zata fasa qirjinta ta fito. Qwaqwalwarta da tunaninta suka hade guri daya suka damule gaba daya. "Itace maganin?.....ta yaya ta zama magani?" Tambayar data sanyata yin shuru kenan tana Jin yadda jikinsa yayi wani irin dumi kaman wanda zazzabi.ke shirin saukar masa. Gaba daya ya dagula mata lisaafi ya kuma dagula mata tunani,ta gaza gane wanne irin lalura ne haka?. "Ta yaya?" Ta fadi a hankali da gasken gaske tana son sani. Kaman jira yake ta fadi,ya sassauta riqon da yayi mata din,yadan janyeta daga jikin nasa a hankali sannan ya sanya dukka tafukan hannayensa guda biyu ya daga fuskartata yana kallon cikin idanunta. "Idan na fada miki......zaki zamarmin maganin?,kinyi alqawari?,zaki taimakeni?" Ya fada a jere idanunsa suna narkewa cikin nata. Yanayin data gani tattare dashi taji ya mata nauyi da yawa. Ya mata abubuwa masu kyau da yawa cikin rayuwarta,duk da har yanzu bata gama sanin wani bangare nasa ba......amma abinda ta sani shi alkhairi,ko yaya akayi maka shi kayi qoqari ka saka daidai gwargwado,ka zama dan halak daidai da abinda zaka iya. (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) "Zanyi......in sha Allah" Wani sanyi yaji yana ratsashi,a hankali yaji ta haura zuwa mataki na biyu cikin zuciyarsa da rayuwarsa,ya lumshe ido yana jin girmanta da kimarta ya dadu. Ya sani......batasan wanne magani yake nema ba......batasan wanne taimako yake buqata ba.....amma kai tsaye ta aminci ta tsaya a gefansa......ta tsaya cikin rayuwarsa. "Muyi sallah.....saina fada miki". " Ka fadamin naga abinda zan iyayi kafin muyi sallar" Amsar data sanya ya bude idanunsa dukka a kanta,yana sake jinta cikin wata qololuwa ta zuciyarsa. Irin wannan attitude yake nema daga mace idanu rufe.....macen da zata aminta zata sadaukar maka komai girman wannan sadaukarwar.....macen da zata aminta ta tsaya kusa da kai......macen da buqatarka zata fara zuwa farko kafin tata....duk da girman buqatar,duk da rashin sanin taqamaimai rawar da zata taka a rayuwarka......irin wannan dabi'un yake nema.....shi kuma ya sadaukar da rayuwarsa da komai daya mallaka,ya qarar da sakanninsa.....mintunansa......awanninsa......watanninsa.......dama shekarunsa na rayuwa gaba daya a kanta. Wani lallausan murmushi ya kubce masa,murmushin daya sake sanya idanunsa suka lumshe. "Idan an kira sallah.....komai ajjiyeshi akeyi har sai anyi sallar....." ".....ina fashin sallah" Ta fadi tana katse maganarsa gami da juyar da fuskarta gefe daya,don a yanzun ta bashi wannan taimakon da yace itace zata iya shine kawai a gabanta ba tare da tasan ainihin abinda yake buqata daga garetan ba. Dif yayi.....kamar kawowa wuta da daukewarta. A hankali yaji jikinsa yana sanyi......komai kuma ya soma narkewa yana fita daga kansa.....ya barshi da wannan daurewar marar da kuma wani zazzabi da yaji yana fara kamashi. Hannunsa ya sanya ya kamo fuskarta a hankali yana dawowa da ita saitin inda yake tsaye. "Har kwana nawa kikeyi?" "Mene haka?" Ta tuhumeshi can qasan ranta ba tare data iya furtawa ba. Zai titsiyeta ta gaya masa abinda ita kadai ya shafa?. "A addinance......ya kamata na sani" Ya fadi yana aza tafin hannunsa gefan fuskarta yana sake tsareta da ido. "Gobe" Ta samu kanta da fadin hakan bawai don ta shirya fadar haka din bane. Ba yau ba ba gobe.....kwanaki da yawa takeso ta cika masa......amma batasan meye a cikin idanunnnan nasa da bata iya masa qarya ba. Zare hannun nasa yayi a hankali yana sauke sassanyar ajiyar zuciya. "Zaki bani magananin?,ba gurin na nanay ba" Ya sake fada a hankali yana takawa da baya da baya zuwa toilet din yana jin gaba daya duniyarsa ta tattara cikin tafin hannunta. "Nayi alqawari.....na yiwa nanay alqawarin zan kula dakai,bada magani bazai zame min abu me wahala ba......idan na dauki alqawari,inaso naga na cika.....kaman yadda idan aka daukarmin nakeso naga an cikamin" Ta fadi a nutse tana bayyanar da wani sashe na dabi'arta da ta taba furta masa karon farko. Ya sani,ya kuma karanci hakan cikin dabi'arta yake.....ko bata fada ba......amma a yau data fada da kanta da bakinta......sai yaji abun ya sake zama cikin kansa. "Dabi'a ce me kyau.....haline me kyau,domin Allah ya fada......alqawari abun tambaya ne" Ya qarashe maganar yana isa bakin toilet din,sai ya juya yana karanta addu'ar shiga bandaki ya saka qafarsa a nutse. Tana da wasu qualities.......tana da wasu dabi'u da ita kanta batasan tana dasu ba. Komai zaiyi baya yinsa kansa tsaye,....komai zaiyi yana binciken ingancinsa. Cikin dabi'unta akwai CIKA ALQAWARI. Bata iya qarya ba,kaman yadda bata iya boye abinda yake cikin ranta ba. Tana bayyana zuciyarta ne saman fuskarta koda hakan baiyi daidai da abinda mutum yakeso yaji ko ya gani ba. *zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 08187255862 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 08187255862 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 72* ____________________________ *_Amintaccen gurin siyayya_* *_ingantattun kaya akan ingantaccen farashin da ba irinsa a kasuwa_* *_BONONZA DA PROMO akai akai_* *dukka sai a HUGUMA CLOSET* *Duniyar kayan yara,mata,maza,dukka* *shaddodi,atamfofi,laces,abayas,jakankuna,takalma,agogo,sarqoqi,English wears,night wears,under wears,da duk wani nau'in sutura babba da qarami* *_Karki yadda ayi babu ke.....leqa kiga yadda closet din HUGUMA kullum ke cike da kaya akan farashi me kama da KYAUTA_* *_YAN SARI....YAN REPOSTING.....DA SARAKAN ADO MASU SIYA DON KANSU....DUKKA INA MUKU MARABA_*🤝🤝🤝🤝 https://chat.whatsapp.com/FrqgC0YmUWP4FPmUzYuLJX __________________________ Izzarta.....wani abu da yayi masa dari bisa dari. Mace me izza a gurin 'ya'ya maza DUNIYA CE. Zai wahala a yaudareta ko a cutar mata ta wasu hanyoyi da basu kamata ba. Zata kamewa miji kanta.....ba namijin daya isa sai MIJINTA KAWAI mallakinta. Zata bashi dukkan soyayyarta saboda shi daya ne ya cancanta ya mallaketa ba tare da wani ba.........uwa uba.........bayan izzarta,ya karanci abinda ya sake fusgarsa shine.......BA'A SAMUN ZUCIYARTA......BA'A SAMUN SOYAYYARTA.....BA'A SAMUN YARDARTA TA SAUQI. Ya tsarawa kansa zama namijin da zai qwace daga hannun Tarin mazaje.....ba wanda za'a kawo masa ko ya samu yana daga kwance ba.... Ya zabi yayi farautar zuciya,....bawai zuciyar tazo ta sameshi a inda yake ba. A nan maganganun omar suka dawo masa. Da gaske ne.....itace kalar macen da yakeso......ba'a halitta kawai ba ko zallar ilimin addini.....aah dabi'u. Wasu kebantattun dabi'u da ba jikin kowacce d'iya mace zaka sameshi ba. Ya kasa son Menelik......ya kasa son saamee duk da tarin qualities da suka hada da kusanci da alaqa dake tsakani.....baisan dalilin hakan ba sai a yanxu. Saboda ya samesu ta sassauqar hanya,qila inda bayan gwagwarmaya ne kamar akhnan.....daya fada masarautarsu cikin tsakiyar yaqi ya zaqulota a tsakiyar sarqaqiyar da batasan tana ciki ba.....a hakan ma tana taurin kai da qi fadin yarda ta zama mallakinsa har sai daya cita da yaqi.....qila ya sosu suma. Da tarin saqe saqe ya daura alwala ya baro toilet din. Tana zaune tana murza yatsun hannunta,tarin saqe saqe ne fal cikin zuciyarta. Ganin fitowarsa ya sanya ta miqe,bai kalleta ba saboda tattalin alwalarsa yakeyi yace da wata dakakkiyar murya. "Karkije ko ina....nanay tace ki kula dani,kin manta?" Komawa kawai tayi ta zauna,shi kuma ya taka zuwa wannan corner din data gani ya sauke hannun rigarsa,ya jawo wata qaramar drawer sai taga ya fidda wata kyakkyawar farar hula irin ta larabawa ya dora saman kansa,ya tattara dukkan nutsuwarsa kamar yana fita daga wannan duniyar zuwa wata sannan ya kabbara sallar. Yadda yake sallar a nutse haka take qare masa kallo a nutse. Karon farko data ganshi cikin qananun kaya,amma sai takeji a duniya ba wani d'a namiji data taba ganin qananun kaya sunwa kyau kamarsa. Ta rasa tsakanin jubah da cloak thobe dinsa da qananun kayansa wanne ne yafi masa kyau?. Abu na biyu yadda yake sallarsa. Yadda yake sallarsa yana sanyata tana jin kamar tata sallar bata karbuwa.....kamar ba daidai take sallar ba,kamar akwai tarin kurakurai a cikin sallartata da abubuwan da ba'a kan daidai take yinsu ba. Ta dauke idanunta tana sauke ajiyar zuciya sanda ya kammala sallar. Tana kallonsa,ya jima saman abun sallar yana azkar da addu'o'i. Karon farko da taji ya sake burgeta,wani iri haske da kwarjini ke fita saman fuskar tasa. Da wannan damar tayi amfani don tasan ba lallai yayi magana ta miqe a hankali zuwa parlor. Tana zaune ita daya daga gefe guda tana lissafin mintunan da suka kwashe cikin dakin ba motsin ko daya a cikinsu. Fitowartata ya sanyata zabura saboda wani abune da bata zata ba. Kallo daya tak tayi mata ta dauke kai tana ci gaba da takawa zuwa saman dining. Kamar itama ta shareta.....kamar kada tace mata komai amma saita tuna bata haka ya cancanci ita ta bullo ba. "Akwai abinda ake buqata?" Ta fadi a taqaice sanda akhnan ke buda warmers din. Cikin ginshira da jan aji irin wanda ya zame mata jiki ta amsa mata bayan shudewar daqiqu kamar ba zata amsa din ba. "Ba aikinki bane wannan" Ta fadi itama a taqaice ba tare data kalleta ba. Tadan jinjina kai,kamar zata sake magana amma ta kasa,saboda yadda ta amsata din da wani yanayi ne na kedin baki da muhimmanci. "Ki danyi nesa kadan da nan,idan da buqatar za'a kiraki......." Maganar akhnan ta biyu ta saukar mata da wani irin nauyi da saida ta waiwaya ta kalleta sannan ta amsa da to. Kalmar to din data fita da qyar daga qasan maqoshinta. Tayi matuqar qoqari wajen zuba komai a qananun bowl,cikin takatsantsan ta zuba a wani qaramin kwando,ta debi magungunan ta zuba akai sannan ta fara takawa tana komawa dakin. Mamaki.......shine abinda ya saukar masa sanda take tura qofar dakin da kwandon a hannunta. Ya miqe a tausashe yana takawa zuwa gareta idanunsa a kanta. Wani irin kimarta tana ninkuwa a ransa. A nan kusa,......bai taba zaton zatayi hidima haka dashi ba. Ya sani bata komai.....komai saidai ayi mata,daidai da zuba abincin,kaiwa bakinta kawai ta sani,amma a yau ta zabi ta kwatanta dafa masa shayi,sannan ta kusanto da abincinsa har daki. "Me zata zama a nan gaba idan ta samu rainon daya dace?" Maganan data sauka a kansa kenan sanda ya isa dab da ita. Hannu yasa ya amshi kwandon idanunsa cikin nata. "Na gode" Ya furta kalmar da wata zababbiyar murya da kuma zababbbun haruffa. Har cikin jininta taji kalmar. "Na gode" To me tayi masa?. Bata manta yadda yake hidima da kai kawon duba lafiyarta ba a duk sanda bata da lafiyar. Idanunsa lumshewa kawai suke suna budewa sanda tayi zaune a gabansa tana zuba masa abincin. Daga yadda yake komai zakasan bawai ta iya bane.....amma ta burgeshi yadda bata sare ba,bata kuma gayawa kanta bata iyaba bazatayi ba. Komai tana qoqarin zubashi yadda taga nayi,tanayi kuma tana gyarawa. Ta ballo magungunan ta miqa masa hade da cup din ruwa. Yafi fari qal din tafin hannunta da kallon wanda har kwanciyar jini sukayi saboda tsananin haske da hutu,sannan ya kalli maganin daya tabbatar ance mata yasha ne kafin abinci. "Bazan sha ba.....banason magani" Ya fadi harda maqale kafada daya. Karon farko da murmushi ya qwace mata,fararen jerarrun haqoranta qal qal kamar qanqara suka bayyana,abinda ya sake jan hankalinsa kenan. Kaman shi?,da girmansa amma yace bayason magani?,kai tana tantama ma. Murmushin daya burgeshi,ya kuma daukeshi ya kaishi wata duniya ta daban. Sai yaji kamar zazzabinsa yana sake ninkuwa,wani abu yana sake kwance masa. Tafin hannun ta maida ta kulle batace komai ba,ta jawo wayarta tahau kiran da baisan wa ta kira ba,har sai da muryar rumaisa ta bayyana. "Da gaske ne......bayason magani?" Iya abinda tace kenan,rumaisa kuma ta gane inda zancan ya dosa. Dariya sosai rumaisa ta saki. "Giiftii.....sai kinyi haquri da obbo.....jinjiri yake komawa nanay idan baida lafiya......bayason magani,gwara a masa allura ko nawa ne da ki bashi tablet yasha. A kan cinyar nanay yake bacci......a nan kusa da ita,itama haka take jinyarsa kamar wata noorah......shagwababben nanay ne". "Na gode" Akhnan ta fada gudun kada rumaisa ta b'aro wani maganan,don tana kallonsa sanda ya sauko ya dawo dab da ita ya zauna,zai kuma iyajin komai da rumaisa din zata fada. Tana kashe wayar suna hada ido. "Tunda an tona miki asiri na.....dole ki zama copy din nanany" Ta fada a tausashe,kafin kuma tayi kowanne yunquri yayi male male saman cinyarta. Kwanciya yayi rigingine,idanunsa akan fuskarta,tadan shagwabe fuska "Idan ba zakasha magani ba....." ".....kece maganin.....na fada miki" Ta katse maganna nata yana lumshe mata idanunsa hannunsa harde a qirjinsa,kamar yadda yake kwance a miqe sambal daga can qasa kuma ya harde qafafunsa suma. ".....kasha wannan din....zan baka wancan maganin duk inda yake za'a nemoshi nayi alqawari" Wani sanyi yaji yana ratsashi,ya sake bude idanunsa sosai a kanta. "Indai zaki bani wancan maganin......zansha wannan......amma ba yanzu ba......sai anjima". Kai ta jinjina a hankali,don ta gagara magana,ya gama kashe mata jiki gaba daya. Wannan kusancin ita kadai tasan me takeji a cikinsa.. (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) Shuru ya ratsa dakin na wasu mintuna,ta dauka bacci yakeyi,sai kuma taji muryarsa a hankali da wata irin nutsuwa. "Khadeeja bint kuwailid" Ya furta da wasu nutsatstsun kalmomi. Bai sake bata daman yin magana ta biyu ba ya sake furta. "Kin taba jin tarihin me sunanki?....khadeeja bint kuwailid,matar manzo ta farko?" Ya qarasa fada yana bude idanunsa fes a kanta. "Aah" Ta amsa masa a nutse,can qasan ranta wani abu yana motsa mata game da son jin tarihin. Numfashi ya sauke a hankali,ya koma ya kwanta saman cinyarta kaman dazun,yana jin wata irin nutsuwa da bai taba samun makamanciyarta koda zai kwanta akan katifar da tafi kowacce katifa tsada a duniya. "Soyayyar da bata da makamanciya har yanzu a tarihin duniya......soyayyar khadeeja bint kuwailid da manzon Allah S A W" Ta kama masa kalmar qarshe suka maimaita tare,wanda bata sake bari ta kubce mata ba tun daga randa ta karanta a tarihinsa falalar yin salati a gareshi a duk sanda aka ambaci sunansa. "Itace mace me daraja...mai qarfin kudi dana iko.....'yar kasuwa irinta ta farko a tarihin musulunci....amma bata daga kanta ga soyayya ba...." Ya furta a nutse kamar me maida numfashi. ".....lokacin da taga abinda takeso" Sai ya sake dakatawa. "......ta zabeshi cikin nutsuwa.....ba hayaniya......ba matsawa" "Kuma bai manta da ita ba ko bayan ta rasu......ya qare rayuwarsa yana ambatonta har a gaban macen da yace yafiso wato nana aisha RA.....ya maimaita mata yana son khadeeja.....ya sake maimaita mata Allah bai musanya masa da wadda ta fita ba......kinsan duk dalilin me yasa ta samu wannan darajar?". Kai ta girgiza a hankali,kwadayinta da son jin cikakken labarin yana ratsata. Idanunsa ya bude sosai a kanta yana dubanta, "Ta soshi sanda kowa ya qishi,ta sadaukar masa sanda kowa ya hanashi......ta rungumeshi sanda kowa ya juya masa baya......ta gasgatashi a sanda kowa ya qaryatashi......ta zabeshi a sanda ta fishi dukiya......ta fishi shekaru......itace kuma uwar 'ya'yansa gaba daya banda guda daya tal a ciki". Sai yayi shuru yana duban cikin idanunta. Shuru ya biyo amma yana iya ganin yadda ta kalleshi har sau biyu. Tanaso tace ya bata cikakken tarihin.....amma kamar mejin nauyin hakan. Murmushi ya saki "In baki tarihin......ke kuma me zaki bani?" Ya tambaya da wani irin coolness idanunsa kamar namejin bacci. Batasan sanda murmushi ya subuce mata ba,.....a karo na biyu ba tare data kawo komai a ranta ba tace. "Komai.....komai da kakeso" Kai ya jinjina sosai,sannan ya gyara kwanciyarsa cikin jikinta. A nutse kuma ya fara warware mata tarihin tun daga farkonsa har qarshe. Tarihin yazo qarshe da kiran sallar magariba dake kwararowa daga babban masallaci zuwa cikin gidan. Sai shuru ya ratsa dakin sai sautin kira sallar. Zuciyarta tayi wani irin sanyi.......wani irin yanayi takeji yana saukar mata. "Khadeeja da muhammad S A W" Ta lumshe idanunta tarihin yana qawatar da ita. Sunan kuma yana sake mata yawo cikin kanta. "Kamar sunana da nasa?" Ta tsinci kanta da tambayar kanta da kanta,saita ware idanunta wani murmushi yana subuce mata. Tunda take kallace kallecenta......tunda take karance karancenta bata taba cin karo da tarihin soyayya me qayatarwa irin wannan ba. Ya miqe a hankali yana jin yadda zazzabinsa yake sake yawa da kadan da kadan. "Zanyi tattaki inje masallaci". " A dawo lafiya" Ta samu kanta da furtawa a nutse. *zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 08187255862 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 08187255862 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 73* Da wani irin yanayi ya tafi ya barta,wani irin sanyi takeji a zuciyarta. Wani wasai takejin zuciyarta,kamar wadda aka bawa kyautar wani abu. Haka kawai takejin wata walwala ta musamman tattare da ita. Tayi sallah saita shiga wanka. Tunda ta shiga toilet din kansa burgeta yakeyi,wani irin gini da har yanzu idan ta kalleshi,ta kuma hadashi da ginin gidan data baro na koyon al'adu mamaki takeyi. Wadanne irin qwararrun engineers ne dasu haka?. Masu wata irin fasaha?. Wanne irin iko ne haka masarautar suke dashi?. Ko ina idan ta waiwaya ba abinda take gani sai luxury. Wasu abubuwan da yawa saita dinga hangen yadda aka narka gold muraran akayi abun ado na cikin parlor da dakin gaba daya. Riga ta saka mara nauyi,tayi magariba tayi isha'i. Har zuwa sannan bataji alamun shigowarsa ba. Taga tex dinsa bayan sallar isha'in. "My doctor....ina tare da baqi 'yan dubiya" Kalmar ta dinga maimaitawa. Yaushe har ta zama likitanshi? Wanne kulawa ma ta bashi?. Ajiye wayar tana sakin ajiyar zuciya,siririn murmushi yana subuce mata. Sai taji tanason bashi kulawa din sama da yadda ya zata daga gareta. "Don ramuwa ga kyautatawarsa.....don godiya ga soyayyar nanay a gareni" Ta fadawa kanta da kanta murmushi yana sake wanzuwa akan fuskarta. Rabonta da abinci tunda rana,wannan ya sanya ta zauna ta debi kadan daga cikin abinda zata iya ci. Sake duba agogo tayi,bata gaji da zama ba.....amma sai takejin kamar tana cikin kewa....kamar akwai wani abu daba daidai ba tattare da ita,sannan kamar akwai abinda zuciyarta take buqata. Ta sauke qafafunta kenan da zummar miqewa don ta wuce daki ta sauya kaya kira ya shigo wayarta. Tadam fidda ido tana mamaki,shehnaz ce.....a wannan lokacin?,saita sauke murmushi ta koma ta zauna tana daga wayar. "Matar nan,nan gaba sai mun fara cika foam Allah sheikh zai bari mu kiraki bama ganinki ba" Idanu akhnan ta fidda kadan,kewar 'yar uwarta yana kamata. Tayi missing rigimar shehnaz......da komai nata. Fadansu da aisa kawai ke iya rabawa. "Ni matsalata dake ko.....sharrinki baya sallah" Dariya sosai shehnaz ta sauke. "Da gaske nake miki......ba kowa ke iya kiran wayarki ya samu ba,kin zama wata ta daban......irin matar eh....." Bata qarasa ba ta sanyasu dariya gaba daya ita akhnan din,irin dariyar data kwana biyu batayi ba. Zama.tayi sosai tana tambayar masarauta dama kowa da kowa,duk da zai wahala rana ta fito ta fadi momma bata kirata ba. Wani lokacin takanji kamar ta yiwa morsa safiyya tambaya akan nanay,amma saita tuna alqawarin data yiwa nanay din,ba zatayi maganarta da morsa din ba har sai lokaci yayi. Hira suke sosai,irin wadda suka jima basuyi irinta ba. "Ina fushi da aisa da gaske shehnaz". "Ki yiwa aisa uzuri......ta shiga wani aiki ne,amma komai idan ya kammala na tabbatar da kanta zata nemeki,ko waya bata riqewa yanzun". Mamaki ya kama akhnan,duk qaunar aisa da waya?, " Wanne irin aiki ne wannan?" "Banace ba....ni kaina batamin cikakken bayani ba". Shuru alkhnan tayi na wasu daqiqu sannan a hankali ta furta. " Allah ya taimaka" Can qasan ranta tana tuna case din sahel couture,abu daya data sani sultane ya gaya mata ta nutsu ta kwantar da hankalinta,shi zai kula da komai,shi yasa bata sake maganarsa ba. "Ya ake ciki mutuniyar?" Shehnaz ta fadi da salon tsokana. "Shehnaz......zaki fara ko?" Ta fada a narke,don ta sani indai shehnaz ta fara magana da irin wannan yanayin,ba shakka saita tuburaka da tsokana. "Na shigesu.....akhnan wacce irin murya ce wannan?.....sak muryar mutumin daya fara soyayya" Ta fadi tana dariya. Karon farko dariya ta qwacewa akhnan,shehnaz nada tsokana da sharri kala kala......amma sau tari tana da saurin dago abubuwa a zahirin ma'anarsu. "Banason iskanci shehnaz" "Tsaya....to me ya faru?don Allah ki gayamin,tsakanina dake akwai Amana fa" Yadda ta marairaice mata ya bawa akhnan dariya wannan karon sosai. "Babu komai magulmaciya" "Na sanki ciki da bai.....nafi tsoronki idan kikace ba komai,har gwara kicemin akwai kuma kiqi cewa komai din.....inaso ko yaya naji wani abu game da sheikh......wannan zuciyar......yayi nasarar sace mana ita?" Har tsakiyar ranta taji maganar shehnaz,wani sirri ne dake danqare a zuciyarta,ko yaya kuma tana buqatar wanda zata fitarwa dashi....ko yaya tanason wanda zasu tattuna tare. "Nace miki fa ba komai......shi baida lafiya ma.....nanay ta bani jinya" Dariya sosai shehnaz takeso tayi,tana sake yarda da maganar nannie da tace dukkaninsu sun girmi akhnan din. Quruciyarta ta dabance a cikinsu. "Aah.....kice kin zama likita kenan,ko kuma dai zuciyarsa kike gyarawa?" Ta fadi tana dariya. Murmushi tayi itama,tana tuna kalmar daya kirata da ita kenan dazu. Kenan likitar daya kirata......tana iya daukar ma'anar LIKITAR ZUCIYA?. Kai ta girgiza da sauri,ta yaya?......bai taba gwada furta mata komai da yayi kamaceceniya da wannan ba,bataga komai da yake alamta mata wannan ma'anar yake nufi ba. Tabbas kulawa......dukkan wani nau'i na kulawa ta sameshi. Kalar kulawar data sanyata ta fara jin kanta daban.....kalan kulawar data sanya ta fara gane girmanta yana sama da yadda ta zata yake a baya. "Bansan me yake nufi ba shehnaz" Ta furta da wani sauti daya tabbatarwa shehnaz har cikin zuciyarta abinda ta fada. Tashi shehnaz tayi ta zauna sosai tana maida yanayinta na nutsuwa. "Bani labari biftuuu.....ba wani abu daya sauya?,bakya jin komai har yanxu game dashi?......kinsan kalar mijin da kike aure akhnan?.....prince ne.....yariman da yake cikin jerin sahun yarima guda goma da sukafi kowanne yarima gata ilimi kyau da qarfin iko na sarauta a duniya......baki taba googling ba?" Mamaki sosai ya kama akhnan,tadan fidda idanu waje kadan. Dama shehnaz ta sani?,tasan wayeshi amma bata taba gaya mata ba?. "Ya akayi kika sani?,me yasa baki gayamin ba?". Kai shehnaz ta girgiza. " Ba lokacin gaya miki wannan bane akhnan,a sannan ba zaki fahimta ba.....amma a yanzu gani ai ya kori ji ko?,mu gyara wannan issue din akhnan please,ki gayamin....." Shuru tayi kawai tana sauraren zuciyarta,zuciyar dake tsalle a qirjinta cikin bugawar kowacce daqiqa.....muddin zata ganshi....muddin yana kusa da ita......muddin zatayi tunaninsa. "Ya gayamin da kansa....yacemin kamar zuciyata tana gayamin wani abu.......amma naqi saurarenta". Wani numfashi shehnaz ta sauke me nauyi. Tana tsananin son kasantuwar akhnan da haisam,wani irin hadi ne da ita akhnan din batasan adadin dacewar da sukayi da juna ba ita dashi. Batasan yadda labarinsu a yanzu haka ya fara trending bane a duniya ba,da wani irin tittle na HADIN AURE MAFI TSADA DA DACEWA DA JUNA A DUNIYA NA WANNAN SHEKARAR. "Kina qin jin me?" "Ban sani ba" Ta amsa da sauri,dariya sosai ta qwacewa shehnaz. "Kin sani kawai kina tsoron fada ne" "Ba haka bane shehnaz ki fahimta mana" "To meye?" Tambayar data tsaidawa akhnan dukkan wani hanzarinta. Bata katse mata shurun ba,har zuwa sanda ta motsa labbanta a hankali. "Idan na yarda......komai zai canza fa kenan shehnaz?". "Me kike jira ne akhnan?,me kike jira?,ki gwada wannan canjin mana.....ina me baki tabbacin alkhairi ne.....ina me baki tabbacin canji ne da zaki gode masa......me kike jira akhnan?" "Nima ban sani ba......amma na sani.....shi bai taba furta komai ba" Wata irin mahaukaciyar dariya shehnaz ta saki har sai da akhnan ta daga wayar tana dubanta. (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) "Lafiya kike shehnaz?" "Ke za'a tambayar biftuuu......ashe?,jira kike sheikh muhammad yace ina sonki akhnan?,sau nawa kikeso ya maimaita fadi?". Kanta yadan daure kadan,yaushe ya fadi?,indai ya fadi ne ita bataji ba......ko sau daya bata ji ba. " Ina sonki akhnan ko?" Shehnaz ta sake fadi. "Ki daina fada please mana shehnaz" "Oh.....kalmar ta fara miki tasiri kenan......tabbacin ya fada sau ba adadi ganewa bakiyi.......mu ajiye wasa akhnan......sirrine wannan tsakanina dake......ki fadamin.....abu mafi muhimmanci ke ki soshi.....ki fadamin......kina sonshi?". Sosai tambayar tayi mata nauyi,sosai tambayar ta ninka adadin tsoro da fargabar dake ranta,ta lumshe idanunta a hankali sannan ta miqe tana tattaki cikin dakin. "Shehnaz....." "Akhnan....." Ta kirata itama da yanayin data kirata dashi. "HAISAM........ina sonshi shehnaz......INA SONSHI......" Kalmar da sunan gaba dayansu suka shige kunnensa sanda ya dora hannunsa kan handle din qofar. Zare hannun nasa yayi a hankali,ya maida qofar data bude ya bameta cikin wata irin nutsuwa da bazata bata daman sanin ankai ga bude qofar ba. Hannunsa da qafafunsa dukka yaji suna rawa,saiya koma da baya da baya a hankali yana zama kan daya daga cikin sofas din da aka qawata hallway din dasu. Bugawar zuciyarsa keyi sosai,wani irin lallausan murmushi ya subuce masa duk da zazzabin da yakeji yana saukar masa,wanda dajin wannan kalmar sai yaji kaman ya ninku. Wacce irin sa'a haka gareshi?,dawa take waya data aminta ta sanar masa da abinda ya gani cikin qwayar idanunta tanata boyonsa?,abinda ta share wata da watanni tana fada da zuciyarta a kansa don kada ta fallasata kota tona mata asiri. Ya fahimci tana kiyaye alfaharinta ne......tana kiyaye alfarmarta ne.....bataso ta zube. "Ba zata zube ba.....wannan alfarmar.....wannan jin kan,wannan alfaharin na diya mace dake cikin jininki bazan bari ya zube ba" Ya fadawa kansa da kansa yana takawa a hankali don kada ta ankara da mutum a gurin yana barin gurin. Da maganganun shehnaz.....doguwar hirarsu da musayen ra'ayin da suka jima sunayi ta shiga ta sake watsa ruwa. Tana tsaye tana brush tana kallon fuskarta a madubi. A yau a karon farko ta fallasa asirin zuciyarta. Gani take kaman ba ita ba,dole a yau ta yarda ta amince ta fara sonshi.....wannan malamin.....matashin yariman nan dake da abubuwan ban mamaki masu yawan gaske. Yana cikin ranta duk gilmawar daqiqa,ya kamata zuwa yanzu ya shigo ya kwanta ko don yanayin jikinsa......amma gashi har sha daya da rabi shuru?. Tayi iya qoqarinta ta hada kayan abincin adan qaramin parlor din dake maqale da bedroom din kafin ta shiga wankan da take fitowa a yanzu. Da karsashinta ta bude suitcase dinta tana laluben kayan Bacci,saidai abinda ta gani ya tsaida mata komai. Wasu irin rigunan Bacci ne da basu da maraba da babu,ajiyayyun breast curves ne dasu bayan silk material din da aka ciwa mutunci aka zabgeshi wajen yiwa gown gown wani irin gata da ado na dinkin alfarma daga babban brand dinnan masu samar da kayan bacci na qasar French. *zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 08187255862 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 08187255862 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 74* Ta jima da burin siyan kayan bacci na brand din,amma koda ta taba dubawa duka saita tarar na amare ne dole ta haqura. A yanzun ma haka ta qaraci dube dubenta,kusan komai ma birra bata saka ba. Ba brush sai a bandakin ta dauki wani,skincare dinta turarukanta duka batasa komai ba. Gantalallun kayan baccinnan da batajin zata iya duban koda idanun morsa dasu bare shi da yake ajnabin halittarta. Ta zauna rai bace ta kira birra amma bata sameta ba,ta gwada kiran dukkan wanda zata kira,amma tamkar hadin baki duk wanda ta kira wayarsa a kashe "Zan hadu dake" Ta fada cikin bacin rai tana tuna haka tayi mata tafiyarsu saudiyya. Dole ta dauki wine color a cikinsu wadda tadan fisu mutunci,duk da gefe da gefanta a tsage suke har gurin cinyoyin. Hakanan ta sakata tana jan tsaki a jajjere,ta qarasa gaban madubi tana kallon kanta. Ta mata kyau iya kyau,wani irin kyau me daukan hankali,wani irin kyau da ita kanta ta gani cikin idanunta,amna ta koma kamar ahlul kitabi,don dukiyar fulaninta kamar zasuyi tsalle su fito ta qirjin nata. Ribbon din kanta ta zare ta soma taje sumarta bayan ta tattarota ta dawo da ita gaba daya kafadar hagunta. Da kallo tabi duka cosmetics din dake kan madubin,komai na tsadajjen kamfanin creed aventus ne. Ta miqa hannu ta dauka tana qarewa cream din kallo. Wani abu na burgewa yana ratsa zuciyarta game dashi "you carry yourself quietly… but it says a lot.” ta fada murmushi yana kubce mata. Komai nasa cikin wani irin sanyi yake bayyana,baya nuna koshi waye.....amma komai yana nuna wayeshi. Tana shafa mayukan zuwa hair da body mist din nasa tana zuqar qamshin,wani yanayi na shauqi yana bin dukka sassan jikinta yana saukar mata da kasala. Ta fesa beard mist dinsa yabi iska ya kuma sauka a hancinta sosai da wani irin yanayi. Murmushi ya qwace mata tana tuna mabanbantan lokuta da take tsintar fuskarta gaba daya cikin lallausan qasumbarsa. Wannan qamshinne.....qamshin da yake hade mata dana jikinsa gaba daya ya maida zuciyarta wasa susutacciya. Duk iya qoqarinta kuwa na kame kanta da danne abubuwa masu tarin yawa,amma hakan yana son yafi qarfinta. Amma zata iya?.....aiki da shawarar shehnaz?. Rigar tafe take da band color dinta da wani siririn pants da igiyace kawai take riqe dashi,ta ajiye band din gefe,ta daga pant din tana kalla sannan ta saki tsaki tana jifa dashi,daidai sanda ya bude qofar dakin sanye da wasu cotton pyjamas wine color,pant din ya sauka gaba daya a fuskarsa. Qamshin creed aventus dinsa da tayi amfani dashi ya fara zuqa a jiki,sannan ya saka hannu yana zare pant din. Sama ya dagashi yana son tantance mene?,daidai lokacin da idanunta suka sauka akan pant din itama sannan suka zarce cikin nasa idanun. A sannan....ji tayi inama qasa tana iya tsagewa biyu ta shige ciki?. Pant dinta a hannunsa?,ya dagashi yana qare masa kallo?. Sai kuma a hankali tunaninta yabar kan nan......tunaninta ya fara komawa kan jikinta sanda taga yana sauke pant din yana aza dukkan dubasa akan gangar jikinta. Da wannan narkakkun idanuwan "This is not ordinary....." Ya fada can qasan ransa,yana jin wani abu da yafi magnet qarfi da girma yana fusgarsa da wani yanayi me tsananin tasiri. Karo na farko a duniya da idanunsa suka taba ganin wani abu mafi daga hankali cikin tarin wannan nutsuwar tasa da kamewa.....qirjinta muraran......bajajjen qugunta.....santala santalan cinyoyinta dake showing kansu ta gefe da gefen tsagar da aka yiwa rigar a duk sanda rigar tadan kad'a. “…you shouldn’t look like that.” ya furta da yaren faransanci da wannan accent din da a yau ya sake fita tartar da wani sauti me kama da mutumin dake gulma bayaso koda na kusa dashi ya jishi. Yayi maganan birkitattun idanunsa a kanta.....saidai nutsuwarsa bata kauce ba.....bata kuma fasa bayyana a tattare dashi ba. Yadda yake dosota kai tsaye ya qarasa karya duk wani kuzarinta. Tsoro ne yakeson mamayeta kuma tanason takawa koda towel dake kusa da ita ta dauka ta rage tsiraicinta daya bayyana......amma sai taji kaman an riqe qafafunta. Takawa yakeyi zuwa gareta,amma yana jin kamar an qara nisan tazarar dake tsakaninsu. Wani narkewa yakejin yanayi tsakanin blue eyes dinta da wine colour din gown din suka cakuda suka bada wani kala na daban. Ya isa gareta,idanunta cikin nasa....idanun dake cakude da tsoro,tana son karantar kowanne motsinsa ba tare daya kufce mata ba. Wata siririyar tazara ya bayar a tsakaninsu,tazarar da taku daya yayi yawa sosai ya cikasheta. Qamshin creed aventus din dake jikkunansu dukka su biyun ya hadu ya cakude dana juna. Bugun zuciyoyinsu dana numfashinsu suka soma qara adadin gudunsu. Wani irin yanayi.....me kashe jiki.....me narkar da zukatan masoya ke dawaniya dasu. Akwai shimfidadden tsoro.....wani nau'in kunya me girman gaske dake lullube da ita,amma hakan bai hanata ganin zallar kyan da yayi cikin wine color din pyjamas dinsa masu silki da taushi ba. Kamar ita ko shi wani yasan kalan kayan da dan uwansa zai sanya a wannan daren.....wannan daren da yazo musu da wani irin yanayi tamkar an wanke qwaqwalensu an kuma jefasu wata sabuwar duniya. Duniyar da bawata halitta me rai DAGA ITA SAI SHI. A hankali taji ya zare siririn band din dake tsakanin yatsunta.....ya kama kafadarta yana juyata tana fuskantar madubin,ya mannata sosai da qugunsa......wani irin abu ya ratsa ta fatarta yana bin kowanne sashe na jikinta yana barin saqo me tsananin nauyi,sannan ya zare kowanne kuzari nata ya watsar gefe. Hannunsa dukka biyun ya sanya,ya tattaro gashin ta gefe da gefen kunnuwanta yana maidashi gadon bayanta kamar yadda ake kame gashin yaro da ribbon,saidai maimakon ya saka band din ya daure mata,sai ya bazashi saman tafukan hannuwan nasa ya kuma nutsa fuskarsa a cikinsu yana shaqar daddadan qamshinsa. Bugun zuciyarsa ya sake canzawa.....fitar numfashinsa ta qara gudu da wani irin adadi kamar wanda yayi wasan tsere da qafafunsa na tsahon kilomitoci. Tunda ya taso ya sani.....kusan dukka qabilarsu suna da tsahon gashi,bama iya 'yan gidansu kawai ba,.....saidai bai taba ganin suma irin tata ba. Bai kuma taba sanin yana qaunar dogon gashi ga mace ba sai ranar daya fara ganin nata karo na farko a rayuwarsa. A ranar ya shiga da sumar cikin list na abubuwan da yake qauna daga matar aurensa. "Bbiif......ttuuu" Ya kira sunanta muryarsa tana wani shaking bayan ya saki dukka sumar ta zuba a gadon bayanta,ya saka hannunsa ta wuyanta ya manneta da qirjinsa yana boye kansa tsakanin kafadunta da wuyan nasa. "Naammmm" Ta amsa a birkice itama,abinda takeji daga jikinsa zuwa nata wani baqon abune da bata taba sanin akwaishi kaf rayuwarta. Uwa uba wani irin zafin zazzabi da jikin nasa taji yana fiddawa. "You make silence......difficult....." Ya fadi a rarrabe yana jin kamar zai iya controlling kansa a yau dinma kamar baya......amma jikinsa qwaqwalwarsa da komai nasa suna gaya masa SUNZO IYAKA. Ido ta lumshe tana jin yadda zuciyarta ke qarasa narkewa,yadda zuciyarta ke qoqarin fita daga mallakinta zuwa tasa ta har abada. "Me yasa biftu......wadannan kayan.....you shouldn’t look like that......kinaso ki jawo naci amanar nanay!?" Ya fadi da dukka zuciyarsa yana hade fuskarsa da tata guri guda,hancinsu ya game guri daya suka fara musayar zazaafan numfashin daya sake birkita nutsuwar kowannensu. "B.....bani bace.....birrrrrrrraaa" Kasa qarasawa tayi saboda tsintar dukkanin tafukan hannuwansa masu dumi da tayi saman dukiyar fulaninta da wani yanayi daya sanyata tafiya zata sulale a gurin,saidai ya saka dukka qarfinsa ya tareta yana sake tsaidata tsaye qyam. Ko nawa zaa bata....kome zaa bata ba zata iya kallon qwayar idanunsa a yau ba. Kwata kwata basu take gani ba.....wani mayunwacin zaki kawai take hange da ya doshi abar farautarsa. "This is dangerous for my focus......me yasa kika saka?" Ya rada mata cikin kunnuwanta,yanayin daya sanya ta damqe kafadarsa da dukka hannuwanta,labbanta suka motsa suna fadin kalmar "Wayyo Allah na bapp....." "Shshshshh......" Ya fadi da wani sauti me qarfin gaske,yana aza yatsarsa saman lips dinsa da yanayin dake nuna qaqqarfan gargadi. "Yau ba bappi.....ba motii.....ba nanay.....ba morsa.....ba kowa....ba kowa sai muhammad.....sai khadeeja" Ya qarasa furta sunanta kamar wanda yasha giya ta soma bugar dashi. Bai bata daman qara tunani na biyu ba ya soma zare dan siririn abinda ya taimakawa rigar ta zauna a jikinta. Ta tabbatar idan ya kammala ba abinda yayi saura da zai boyu a jikinta........komai zai bayyana......idan tace komai tana nufin komai da komai din,don haka ta damqe hannunsa da sauri tana girgiza masa kai. "Bakuyi haka da bappi ba......" "Ba haka kika cewa nanay ba....." Shima ya fada yana dora hannunsa saman nata hannun da take cukuikuye da gaban rigar. Yadda taga fuskarsa dukka tayi jajur kaman ya shafa wani abu......lips dinsa suna rawa kaman wanda aka watsawa ruwan qanqara sai tsoro ya sake kamata. Wannan fitar numfashin nasa dake bata tsoro a yau yafi na koyaushe fita da wani irin tsananin gudu da qarfi. "Na shiga uku!" Ta fada hawaye suna balle mata. Wannan abun tsoro yake bata.....ta soma fahimtar inda ya dosa. Wannan abun da maleek ya yiwa falaak ta kusa mutuwa?. (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) Durqushewa ya tafi zaiyi saboda wani kartawa da mararsa tayi yana fadin. "Ya salaaaamm" Yadda ya sake mata rigar da sauri yana damqe cikinsa ya sanyata ta gigice gaba daya. Ta manta da wani batun riqe riga ta soma qoqarin riqeshi a gigice tana tambayarsa "Mene ne?,cikinka?....kayi haquri don Allah......sannu" Dukka a rude tana rasa abinda zatayi masa,sai kawai ta jawo masa kujera gabansa tana cewa. "Ka zauna?,zaka iya ko na daga ka?" Duk da tsananin zugi da yake ciki amma yaga yadda fuskarta ta soma jiqewa da hawaye,hakanan maganarta ta qarshe kota dagashi?,ba qaramin dariya zata sanyashi ba inda lafiya yake. Da wanne qarfin?da wanne karsashin?,tana tsoron a maidata mace cikakkiya ina taga qarfin dagashi?. Ta ajiye masa ruwan sanyi,ta ajiye masa ruwan dumi.....ta kawo tissue. Dukka a rude take,a yanzun bata kanta take ba,yadda taga yana murqususu kawai ya daga hankalinta. Kuka take mara sauti,ya riqe hannunta sosai kuma ya hanata fita bare taje ta nema taimako na magani ko asibiti. A qalla mintuna ashirin sukayi a haka kafin ya soma lafawa. Gumi yake sosai,don haka bai musa ba ya karbi ruwan sanyi data zuba ta miqa masa. Koda yazo karba hannuwanta rawa suke,tausayinta sosai ya kamashi. Inama zai iya kauda mata kai ya rabu da ita?,inama a yau zai iya haquri?,saidai ya sani a wannaj lokacin.....haqurinsa daidai yake da komai ya sameshi,don a zaunen da yake yana jin yadda mararsa takeyi kaman zata tsage. Wannan karon ita taqi sakar masa hannun,ta riqe hannun nasa sosai cikin nata. Ya daga idanunsa a hankali ya kalleta "Sannu" Ta sake fadi muryarta na rawa a karon da babu adadi. "Wanne magani ne.....don Allah ka fadamin zan baka.....karka mutu....nanay......" Saita kasa qarasawa ta sake masa kuka. Tsam ya miqe,ya dagata cak ya dorata saman dressing table sannan ya jawo kujerarsa gaban table din qafafunta suna gogar nasa. Kallo yake qare mata sosai,yana lissafa shekarunta cikin kansa. Tayi qanqanta da daukan dukkan wani bala'i da qulle qullen mammina......bai sake gasgata hakan da gasken gaske ba sai a yau. Da gaske batasan komai ba sai qanqanuwar duniyarta.....izzarta da sarautarta. Duka duka shekarun daya bata a baya ma yanzu ya sake zabgesu. Ba duka 'ya mace bace zaka tara a zamin nan bata gane komai sosai game da wannan mu'amalar. Yau ga guda daya a gabansa,abinda ya ninka hauhawar farashinta a zuciyarsa. A yau yakejin ya shirya maidata tasa cikakkiya.....a yau yakejin ya shirya sanyata taji cewa ta zama tasa halak malak......a yau yakejin koda mutuwa bazai bari idan yana da iko ta qwaceta daga hannunsa ba. "Kina da magani akhnan....kina dashi". " Wanne ne?" Ta fada da sauri tana share hawayenta. Kansa ya dora sosai saman cinyarta yana zagaye mazaunanta kamar yadda ta lura hakan yana masa dadi,saita cusa yatsunta itama cikin sumarsa,abinda ya sanya wuta ta dauke masa na wucin gadi. Fatanta kawai gari ya waye ta bashi wannan maganin nanay ta yaba da qoqarinta. Shima ya yarda ta rama halaccin da yayi Mata a baya "Ka fada....don Allah" Ta fada a raunane. Kansa ya daga sosai dab da fuskarta,ya sanya idanunsa cikin nata. "Kin shirya yadda mu cika aurenmu?.....kamar yadda kowanne ma'aurata suke cika aurensu?.....kin shirya yadda ki mallakamin kanki na.maidaki cikakkiyar mace?....." Ta tabbatar inda da wani abu daban aka gina zuciyarta da qirjinta ba abinda xai hana a yau su tarwatse su fado,tsoro firgici da razani suka sanyata kauda kanta da wani irin sauri,saidai bai bari ta cimma nasarar hakan ba,ya sanya hannunsa ya juyo da fuskarta zuwa gareshi yana dorawa da. "Alqawari.......alqawari kikayi.....kince indai kikai alqawari saikin cika.....kince zaki kula dani wa nanay.....kince zaki cika wannan alqawarin...... Biftuuuu......." Ya qarashe maganar da wani irin rarraunan rauni daya shiga zagwanyar da abinda yayi saura na qarfin zuciyar daya rage mata. 🥹🥹🥹🥹🥹🥹 Ba'a riqe amanar nanay ba da alama,Allah yasa ka tanadi kalaman da zaka mata bayani a gobe idan Allah ya kaimu. Nidai da luu luu royal readers ba ruwanmu🏃🏽‍♀️🏃🏽‍♀️🏃🏽‍♀️🏃🏽‍♀️🏃🏽‍♀️ *zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 08187255862 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 08187255862 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 75* ___________________________ *_Mg's ORGANIC SOAP_* *_Shin kin gaji da banke banken sabulu wa fatarki?_* *_Kullum ba ci gaba?_* *_Kullum jiya iyau sai sake lalacewa ma da takeyi?_* *_matso maza ga maganin matsalanki da izinin Allah_* *MG'S ORGANIC SOAPS* *_kamfanin da ya shirya tsaf don samar miki da sabulun da zai sanya fatarki KYAU ta goge tayi haske ME AJI bana bleaching ko me bata fata ba_* *_KALAN 'YAN ABUJA.....kalar hutu hajjaju,asalin kalar fatarki ta anihin_* *_Masu matsalan SKIN irinsu PIMPLES,SPOT,ACNE,SUNBURN in sha Allah kukanku ya qare....matsalarku ta qare_* *AKWAI PACKAGE DA SUKE HADAWA GAME BUQATA* *yammata.....zaurawa....amare.....da iyayen gida masu capacity wanda ya hada da* Soap Facewash Face cream/body cream Scrub Serum Cleanser Glow oil Toner *duka cikin package din* *_INA MASU FAMA DA NANKARWA(STRETCH MARK)MG'S ORGANIC SOAP bata barku a baya ba_* *Ku nememu kai tsaye a wannan number don GYARA DA MAGANCE MATSALOLIN FATARKU* 0806 299 1549 *MG'S ORGANIC SOAPS* *_takenmu (MAIDA TSOHUWA YARINYA....A SABUNTA YARINYA ZUWA SABUWAR HALITTA)_* ____________________________ Gaba daya ta qarasa gigicewa da maganarsa.....wannan alqawarin?.....da gaske ita ta daukeshi.......ita tace zata bashi maganin.....ita ta furta da bakinta. "Amma garin yaya?" Ta yiwa kanta tambayar tana girgiza kanta gami da matse hannunsa da kyau cikin nata ba tare da tasan tayi hakan ba. "Bazan iya ba......mutuwa zanyi.......bansan......bansan....." "Shikenan?.....shikenan.....zan barki.....ni na yarda na mutun,amma karki manta idan na mutu.....na rataya a wuyanki biftuuuu.....nanay zata kalleki a matsayin wadda kika gaza.....kin kasa kula mata da yaron ta,nima zan mutu ina tuna cewa khadeeja ta kasa cika alqawarin data yiwa muhammad" Ya qarashe maganan a wannan karon shike riqe da hannunta idanunsa yana sake nutsasu cikin nata. Idanun da a yau wasu dabanne ba irin wanda ta saba gani ba.....wani irin ido ne da yake fidda wani narkakken qyalli me garai garai a cikinsa. Idanunta ta lumshe saiga ruwan hawaye yana gangarowa,ya sake matsawa da kujerarsa jikinta sosai har gwiwoyinta suna shigewa cikin qirjinsa. "Karkiyi kuka.....na gwammace na mutu d......." "Ba zaka mutu ba!" Kalmar ta fita tana fusgarta da qarfi daga bakinta. Kalmar MUTUWA na daya daga cikin abinda ta tsana,tun daga sanda ta fahimci ita ta rabata da mamminta bayan kowan data sani tare da tashi mahaifiyar yake raye. "Zan mutu mana khadeejaaaaaaaa......" Yaja sunan numfashinsa yana yin Kamar zai dauke saboda mararsa data sake dunqulewa ta cure guri daya da wani irin ciwo. "Ba zaka mutu ba!." Ta sake fadi a wannan karon muryarta tana fita da sautin kuka. Miqewa yayi tsam a gabanta,ya bude tafukan hannunsa yana sanya nata a ciki ya mayar ya kulle,ya sake matsowa sosai yana cike gap din dake tsakaninsu ta hanyar kusanta fuskarsa da tata. Da wata irin murya.....wata narkakkiyar murya da sam batayi kama da tasa ba,wata kalan murya dake fita daga can qasan maqoshinsa gauraye da wani irin sauti me nauyi taushi da sanyi ya furta. "Kina sona biftuuuu" A dan razane ta daga idanunta tana kallonsa. Wannan tsoron ya gauraya da wata matsananciyar kunya. Ya akayi?,abinda take tsoro?,abinda take kunya?,abinda take boyo ya sani gashi a tsaye gabanta da mafi girman kusanci yana gaya Mata shi kai tsaye. "Kamar yadda nake MUTUWAR QAUNARKI!!" Ya furta yana motsa labban nan nasa da suka sake zama wani pink color sosai yana dage mata dukkanin girarta,lumsassun manyan idanunsa suna sake nuna girmansu. Wani irin mamaki ya finciketa yana barazanar tsayar mata da numfashinta. Idanunsa take kalla kai tsaye kamar yadda shima nata idanun yake kalla,yana jin kamar ya shige ta cikin idanun ya saje da ita,su kuma narke su zama abu daya ita dashi. "Yes......ina mutuwar sonki gimbiyata.........ina sonki.....ina sonki.....ina sonki.....ina sonki......ina sonki....ina sonki......" Ya maimaita sau ba adadin da sai data ji kowacce wuta ta jikinta taka tsinkewa......ya maimaita kalmar da dukka zuciyarsa da fitar numfashinsa......ya maimaita fada da yanayin da a cikin muryarsa ta dinga jin kamar numfashinsa zai dakata daga fita daga hunhunsa,ya sauke kalmar yana kuma sake dorawa da fadin. "......ba don wannan lokacin ba......ba don wannan ranar ba.....ba kuma don ina neman komai ba........biftuuuu........ina sonki tun daga ranar dana fara gane wacece ke!......tun daga wancan ranar,.....tun daga wancan lokacin,ban sake bacci da idanu biyu ba......ina sonki.......ina qaunarki irin yadda baki da dukkan kalamai sunyi kadan su bayyanata a asalin yadda take a zuciyata". Wani irin sheshsheqa ta saki......irin sheshsheqar yaron da yasha kuka me yawa da tsaho ya kuma samu lallashi. Nauyi taji kalaman sun manta,tamkar wannan jaririyar zuciyar tata ba zata iya daukarsu ba. Yana mata magana da wani irin yanayi daya qarasa illata zuciyarta ya kuma kassarata gaba daya. A cikin kunnenta......cikin tsakiyar kunnenta bayan ya dora labbansa ya furta kalaman. Tamkar dai kalamai ne da sukafi komai daya taba furtawa a duniya daraja da tsada.....irin kalaman da ake bada ajiyarsu da wani irin girma martabawa da darajtawa zuwa ga kalaman.......wadansu kalamai da suka zama zababbu na musamman da ba kowanne kunne ya cancanci yaji irinsu ba. Kalaman da akeso kuma su isa kai tsaye zuwa ga ZUCIYA inda ke fafutukar kafa kai a can. Ya saukesu a muhallinsu,ya kuma saukesu a inda ya dace,sun kuma yi wata irin sauka da cikin qasa da second goma suka kafa wasu irin rassa masu matuqar qarfi da tunbukesu zai zama wani abu mafi girman aiki da dan adam zai tunkari yinsa. "Ki yarda ki zama MALLAKINA.......kiyimin alfarma gimbiyata" Ya qara fadi yana narkewa cikin jikinsa kamar yadda yaro me qyuya yakeyi sanda wani ke yunqurin karbarshi daga hannun mamarshi,yana sake matse tafukan hannayenta cikin nasa. "Nnnnnnnn.......na amince.....amma don Allah.....kada ka kasheni......kad......kada ka cutar dani....mmmn" Bata qarasa fadin maganarta saman dressing table din ba sai bisa hannuwansa. Ya dagata cak kamar yadda uwa ke daukan jaririnta da tafukan hannayenta gaba daya. Ya hadeta da qirjinsa,yana sunkuyo da fuskarsa daidai tata,wani abu da batasan meye ba yana taruwa cikin idanunsa. "Kinyi hannun riga da cutarwa daga kowacce irin halitta tun daga wancan lokacin......koda kuwa aljani ne komai girman sharrinsa ballantana dan adam.......dan adam dinma yaron nanay da motii?.....ZUCIYARKI nakeso ki mallakamin ba iya gangar jikinki ba......kin shirya mallakamin gaba daya?". Wannan yanayin yafi qarfinta.....wannan kallon.....wannan kalaman......wannan idanun duka sake kasheta suke sakeyi bayan kowacce daqiqa. "Ki mallakamin......don Allah......na roqeki" Ya fada muryarsa tana rawa sosai yana kuma manne fuskarsa da tata. "......Na mallaka maka.......na baka" "......har abada?" ".......har abada" Ta maimaita tana gyada kanta a hankali. "Idan nace na gode......tabbas na rage martabar kyautar da kika yimin......zan maidake mallakina da gaske ba'a baki ba......zan tabbatar kin zama tawan......sannan nasan wadanne zababbun abubuwa ya kamata a gode miki dasu.......amma saidai......" Ya fadi da wani salo na rad'a,irin radar nan da murya ke fita a dakushe bada cikakken sauti ba. "......ki zama jaruma.......don Allah biftuuuu.......bazan cutar dake ba........amma banyi alqawarin iya riqe kaina gaba daya ba". Daga haka yaci gaba da takawa yana riqe da ita a hankali kai tsaye zuwa bathroom. Ajiyeta yayi saman wata waterproof chair,wadda kusan amfaninta cikin bandakin kawai shine zama. Zaman tayi kawai,tana kallon yadda ya daura alwala,alwalar da duk bayan wasu sakanni sai ya waiwayo ya dubeta kamar zata bace masa. Gabanta ya tako a hankali da wani abun diban ruwa. Cikin salo na girmamawa ya dawo gabanta ya tsugunna saman qafafunsa "Kiyi alwala" Ya furta da wata irin kasala yana duban qwayar idanunta. Ruwa ya dinga zuba mata a hankali tana daura alwalar harta kammala. Ya maida abun,ya kuma ciro qaramin lallausan towel ya dawo gaban nata ya sake tsugunnawa. Qafafunta ya kama ya dora saman cinyoyinsa,ya saka towel din yana tsane mata ruwan cikin kulawa da wani irin taushi,toilet din ya dauki wani irin shuru sai zuciyoyinsu dake bugawa cikin qirjinsu da wani irin yanayi. "Ina fatan wannan rana ta zama mabudin alkhairi tsakaninmu......alkhairi na har abada" Ya fadi yana sanya mata towel din cikin tafin hannunta don ta qarasa tsane damshin,saboda baya jin zai iya tsane mata na sauran sassan jikinta ba tare daya rasa alwalarsa ba. Shi ya zura mata after dress....sannnan ya mata rolling da mayafin abayar. Fuskarnan ta fito tas da wani irin kyau haske da sheqi kamar farin wata. Ya zare idanunsa yana sake qoqarin tattalin alwalarsa,ya matsa zuwa gaba ya tayar da kabbarar sallah. Raka'a biyu sukayi,bai tsawaitasu ba,kaman yadda bai tsawaita addu'o'in ba,ya juyo yana dubanta yana zube mata idanunsa da suka sake wani laushi. Hannunsa ya aza saman goshinta,a hankali cikin nutsuwa labbansa suka fara motsawa. "Allahumma inni as'aluka khairaha wa khaira ma jabaltaha alaihi......wa'a'uzubika min sharriha wa sharri ma jabaltaha alaihi". Yana qare addu'ar wata irin nutsuwa tana saukar mata. Wata nutsuwa me cakude da aminci tana sassauta wannan tarin fargabar dake maqare cikin zuciyarta. (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) Ya cire hannunsa daga saman kanta,dukkanin jikinsa yana amsawa da wani irin yanayi,saidai duk da hakan.....zaiso ya gina dare me albarka.....zaiso ya bude maqullin gina nashi iyalin na qashin kansa da dukkan wani abu na koyi da sunnar manzon Allah S A W,domin neman albarka a cikin rayuwarsu gaba daya. Tana kallonsa ya fita......ba jimawa kuma ya dawo daki dauke da wani dogon glass cup. Dab da ita ya zauna,yana aike mata da saqon wannan lallausan qamshin nasa da a duniya a yanzu ba wani kalan qamshi da take mutuwar so da marari irinsa. Da tattausan murmushi akan fuskarsa ya miqa mata cup din,wanda sai a sannan ta lura madara ce a ciki. Tatacciyar madarar data lura qabilar oromo na matuqar ji da ita. Madarar da sha daya ta mata ta samu kyakkyawan mazauni a cikin zuciyarta.....sannan kuma ta fahimci tarin banbance babancen dake tsakaninta da tasu ta agadez. "Bismillah......kada kice a'ah.....late comer ne ban shigo da komai ba" Ya fadi dukkanin idanunsa da jikinsa na sake masa nauyi. Saidai akwai abinda yakeso.....wannan TSORON.....wannan tsoron yakeso ya cire daga ranta,nutsuwa yakeso ya samar mata. Ba gangar jikinta kawai yake buqata ba.....a'ah.....harda wannan zuciyar dake adane cikin gangar jikin. Yanaso ya gina darensa da wani memory me kyau......yanaso ya fara da qauna soyayya da kulawa,ta yadda ba zata sake gudunsa ba,daga wannan ranar.....daga wannan lokacin,zasu narke ita dashi,su zama abu daya wanda ba za'a iya banbance ina HAISAM ba ina kuma AKHNAN?. Bata musa ba,ta saka hannunta zata karba,saidai ya mata dabaran hade yatsunta cikin nasa,bai kuma sakar mata hannun ba ya tayata kai cup din bakinta. Kurba daya,biyu uku tace alhmdlh,bai matsa ba sanda ta zare hannunta,sai shima yakai cup din bakinsa saitin inda ta cire nata bakin. Kurba ukun kawai shima yayi,ya miqe dashi a hannunsa ya sake fita. Ta sauke ajiyar zuciya me nauyi tana jin nutsuwa na sake saukar mata. Wannan tsoron firgicin da razanar da tayi a dazu yana raguwa a hankali. "Ashe ba haka bane....ba kaman yadda na zata bane" Ta fada can qasan ranta. Da cikakkiyar sallamar data sake wanzar da nutsuwarta ya dawo dakin. Yadan jima kadan ba kaman fitar da yayi dazu ba. Ta daga kanta da nufin amsa sallamar saidai kallonsa a yanzu ya gagareta,bugun zuciyarta kuma ya nemi komawa da gudunsa kamar dazun. Ba komai a tare dashi dai gajeran wandon daya tsaya iya cinyoyinsa. Wannan faffadan qirjin.....wannan ginannen jikin.....wadannan fararen cinyoyin dake lullube da baqar gargasa gaba daya sun bayyana. A nutse ya dinga bin kowanne haske na dakin yana kasheshi,kafin ya tako zuwa inda take a hankali. *zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 08187255862 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 08187255862 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 76* ___________________________ *_INA MASU SON KOYON SANA'AR DATA SHAFI ZAMANI KAI TSAYE?_* *_SANA'AR DA A YANZU DA ITA AKE DAMAWA?,ITACE TAKE KAI DUBBAN MATA GA GACI?....MAZA ZO KIYI JOINING WANNAN CLASS DIN DA GUDU_* Wa.me/2348036027448 A cikin wannan class ɗin zaki koyi: ✨ Stone Lifaya ✨ Stone Veils ✨ Glitter Lifaya ✨ Glitter Veils ✨ Paint Work ✨ Flower Design on Lifaya & Veils ✨ Stone Placement Techniques ✨ Glitter Pattern Design ✨ Color Combination & Finishing ✨ Materials Selection Guide ✨ Pricing Your Work for Profit ✨ How to Get Customers Online ✨ How to Start Your Own Lifaya Business 💎 Daga beginner har zuwa professional level. _____________________________ Dukkanin hannuwansa biyu ya saka ya tasheta tsaye tana facing dinsa,ya sanya hannunsa ya fara ware rolling din dashi yayi mata shi a dazu a nutse sannan ya jefar da mayafin a qasa yana jin komai nata ya soma fusgarshi. Hannunsa ya sake sakawa yana zuge zip na after dress din da wani irin slow motion daya dinga tafiya da bugawar zuciyarta. Ko ina na jikin ya soma daukan rawa,tana hangen wadannan qwayar idanun nasa ta siririn hasken daya rage na gefan gado bai kashe ba. Kaman zata iya daurewa sanda ya kammala zuge after dress din ya sabuleta qasa tabi ta qasan qafafunsu.......ya kuma fara balle maballin dake tsakiyar breast dinta wanda shine kawai abinda ya riqe rigar.......amma sanda ya balle na farko ya tafi na biyu saita samu kanta da damqe bayan hannunsa cikin tafin hannunta. Tsaiwa yayi cak idanunsa suna sake rufewa,numfashinsa yana sake hautsinewa da wani zazzafan yanayi. "Banyi brush ba" Ta fada muryarta a rarrabe da yanayin da zai gaya maka ba wannan uzurin bane ainihin silar maganarta ba. Murmushi ya saki a hankali,wani tattausan murmushi da taji saukarsa har cikin tsakiyar zuciyarta. Bata ankara ba tayi gaba daya ya janyota yana raba qafafunta da qafarsa guda daya,ya riqe fuskarta da kyau cikin lausasan tafukan hannayensa......ya kusanta fuskarta da tasa sannan ya fara magana da sautin daya dinka aike mata da qamshin mint me sanyi dake fita daga harshensa "Inason komai naki.....komai naki ki barshi a yadda yake.....ni yayimin......inason kayana a haka......" Ba wannan takeso ba.....uzuri takeso ya bata,kuma a wannan lokacin bata hangeshi ba.....bataga alamar samunsa ba,amma bata saare ba,jikinta dukka yana kyarma sanda taji jikinsa ya fara gogar nata. "Amma......amma ai in......" Bai barta ta sake cewa komai ba,bai bata kowacce irin dama ba ya manne bakinsu guri daya a haukace yana danneta da wani irin zazzafan kiss...... Da wani irin zafi ya sanya yatsansa d'aya ya balle mab'allin daya rage.....maballin daya zame masa shamaki gurin haduwar fatar jikinsu guri daya,sannan ya zura yatsunsa biyar yana sabule rigar data tsaya a iya kafadunta,take ta sulale da sulbin da take dashi tabar masa akhnan dinsa ita d'aya kaman yadda yake da buri da muradin jinta. Wani irin abu taji yana yawo cikin kwanyarta sanda ya manne fatar jikinsa cikin nata......wani irin daukewa numfashinta yaso yi amma ya zuqo mata shi ta cikin zazzafan kiss din da yake aike mata. Wani kalan kiss da batacin karo da labarin irinsa ba......kowanne lungu da saqo na cikin bakinta yake yawatawa tamkar wanda yayi ajiya yake neman inda ya boyeta. Tangal tangal suka fara yi shida ita sanda ya fara bata wani irin skin to skin therapy daya sanya tsigar jikinta gaba daya miqewa,ta kuma fara loosing nata control din. Duk jikinta ya karbi saqonsa da wani irin qarfi da harbawar da bata taba zaton akwai wannan connection din da zai karbi irin wadannan saqonnin a jikinta ba. Tana yin baya luuu saboda karyewa garkuwa jikinta dama karsashinta,da kuma nauyinsa da yakeso ya sakar mata......shi kuma yana gaza tallafota ne saboda nasa qarfin da yayi matuqar rauni da yadda yake sake nisa da duniyarmu......yake kuma sake fita daga hayyacinsa. Wani irin numfashi kawai yake fitarwa da wani irin sauti da yake sake shiga kunnuwanta yake qara haukatata.....a haka suka ta riski bango.....sai yaji kaman dakin ya musu kadan ita dashi.....sai yaji kamar iskar dake duniya ta masa kadan gaba daya. Yadda ya dauketa cak a wani mugun haukace ya sanyata riqeshi gam tana runtse idanunta. Sai a lokacin ta samu bakinta daya zame daga nasa yana nufar saman faffadan gadon dake d'ame da wasu irin shimfidu da alfarma. "Don Allah......" "Karki cutar dani.....karki kiramin kowa......don Allah nima" Ya fada bayan ya mata kyakkyawar shimfidewa saman gadon,shimfidewar data bashi daman ganin komai da komai,kaman yadda yakeso.....kamar yadda ya jima yana mafarkin samu da gani......shimfidewar data sake haukata kowanne sashe na kwanyarsa,ta soma tureshi daga duniyar da yake ciki zuwa duniyar isa ga ainihun DUNIYAR D'IYAR SULTANE. A wannan lokacin.....a maimakon duvet shine ya zame mata cikakken bargo,ya maye duk wani gurbi da muhallin da take rungume pillow......ya mamaye kowanne gurbi da take amfani da sutura wajen killace jikinta,ya mamayeta da wasu irin saqonni.....wani irin aike da bata taba sanin akwai irinsa a duniya ba. Hannayensa takeji a mabanbantan gurare a jikinta. Duk inda kuma yayi aike dasu saita rasa numfashinta na wasu daqiqu. A hankali.....cikin nutsuwar da akowanne yanayi bata rabo dashi ya soma fitar da ita daga hayyacinta. A wannan lokacin ya gaya mata KEMA MACACE CIKAKKIYA.....a lokacin ya karanta mata amma a aikace tana da feelings irin na kowacce halittar diya mace lafiyayya. Dishi dishi take ganinsa ta cikin idanunta,tana son tayi magana.....tanaso tace wani abu....tanaso ta dakatar dashi saboda can qasan ranta tana jin kamar ba daidai suke aikatawa ba amma bakinta ya gagara buduwa. Iya ganinta a wannan yanayin kawai ya kunna wata irin wuta cikin kansa,a hankali ya soma sauka daga wancan layin ya fara nemawa kansa mafita. Mararsa yakejin kamar zata fashe...kamar bazai iya qara minti daya a duniya ba. Saidai daga sanda ya fara canza layi......daga sanda ya fara sauka daga wancan karatun zuwa wani....daga wannan lokacin ta fara dawowa hayyacinta......daga lokacin ta gara gane me takeyi.....daga lokacin kuma ta fara gane wacece ita. Shi da ita gaba daya jikinsu wani irin rawa yake kaman wadanda sukayi wanka da ruwan sanyi sanda ake tsakiyar hunturun sanyi. "Kayi haquri.....don Allah" Kansa ya girgiza yana yunqurin zame hannuwansa daga cikin nata. "......idan na haqura,mutuwa zanyi.....Allah mutuwa zanyi da gaske" "Nima zan mutunne.....idan kayi zan mutu HAISAM" Ta furta sunansa da cikakken haruffan da suka sake kunnashi.....suka tsokano wani abu dake danqare can qasan zuciya dama gangar jiki "......sake fada.......HAISAM!" Yayi maganan kamar wanda ya samu tabin qwaqwala yana duban idanunta da fuskarsa data sauya kamanni,yana kuma maimaita sunan nashi da kanshi kamar meson banbance wani abu.....yanajin yadda ta fadi haruffan sunan nasa a jejjere suna kwance wani abu can cikin kansa. "........ki yarda mu mutun tare.....ina da tabbacin zamu sake tashi tare....mu sake rayuwa tare......na miki wannnan alqawarin" Ya fada tana mata wani irin mahukaciyar runguma yana jin har yanxu baikai inda yakeso ba. "Bappi na....k" "Shshshshsh....." Ya fadi yana daga fuskarsa da sauri yatsansa saman lips dinsa. "Nima ina da nanay......ina da motii......amma yau khadeeja nake buqata......ita nafi buqata.......idan sadakin bappi yayi kadan.......a shirye nake na ninka kowanne qwara daya sau adadin dukka abinda aka bayar......a yanzu,ki zabi komai......ki zabi kowanne adadi,na sani tabbas kimarki ta d'ara haka.....ba wanda nake buqata.....sai khadeeja..........khadeeja kawai kawai nakeso........" Ya fada yana sake riqe fuskarta sosai saitin nasa suna musayar numfashin da dukkaninsu yake fita da wani irin qarfi. Yanaso yace mata ta fahimceshi ne.......ta nutsu,amma dukka kalaman sun qwace daga bakinsa,ya gaza samun hanyar da zai sarrafasu cikin bakinsa,duk ta yadda zai gaya mata sai yaga kaman sunyi kadan......kamar ba zasu isar da ainihin abinda yakeso ya fada ba. "Tsoro nakeji...." Ta fada cikin kuka tana jin yadda ya danneta sosai. Tana jin yadda qamshinsa dumin jikinsa da komai nasa a yau yake samun wani irin kusanci da gangar jikinta. Kwarjininsa da wannan birkicewar gaba daya sun hadu sun maidashi wani haisam na daban,wani haisam din da abaya bashi idanuwanta suke kallo ba. (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) "Muhammad zai amintar dake......" Ya fadi yana dora yatsarsa saman lips dinta da yakejin kamar zasu zautashi. Sirara dasu da suka matuqar qawata bakinta,saidai suna da wani irin sulbi da taushin dabai taba jin komai da irin wannan yanayin ba. "Karkaci amanar........" ".......lada Allah zai bamu....kayana ne.....halal dina ce ke biftuuuuuuuuuuu......" Ya kira sunan nata kamar me shirin sumewa saboda yadda numfashinsa ya tafi ya dawo cikin wani irin yanayi na fitar hayyaci. Yadda ta motsa da zummar dagowa ta qwace kanta......wannan motsin sai ya zamana kamar ta tsokaneshi ne.....kamar ta turo masa komai da komai ne......abinda ya sake haukatashi kenan,ya sake toshe bakinta da nashi sannan ya sake dorata akan hanyar data sauka dazun cikin wani irin salo....cikin wata irin siga ta qwarewa tare da sanin kowacce siga ta haukatar da d'iya mace a wannan fagen.....kamar yadda ya karanta a karance sau babu adadi,kafin sannu a hankali ya soma shigar dasu wannan duniyar. Duniyar aminci......duniyar yarda.....duniyar sallamawa......duniyar dake cike da halacci da maida juna abu GUDA DAYA TAK!. Duniyar da ba kowa a cikinta sai ma'aurata guda biyu.....duniyar dake cike da wani irin yanayi dayakan girmi tunani ko shekarun mutum. Wani irin kuka ta saki sanda takejin wani baqon yanayi a tattare da ita. Ba baqon yanayin kawai ba.....wani irin zafi radadi da azabar dake ratsa kwanyarta. "Kace ba zaka cutar dani ba.....amma kasheni zakayi da gaske kaima" Bai fasa abinda yakeyi ba,kaman yadda bai fasa riqe fuskarta cikin hannunsa ba yana girgiza mata kai kamar zautacce,kalma ko daya ta gagara fita daga bakinsa,so yake ko yaya ya gaya mata yadda yakeji.....so yake ko yaya ya mata bayanin da zata gamsu,amma ya kasa fadin komai,sai rawa da dukka ilahirin jikinsa yakeyi,ya gaza riqe kansa sam.....kowanne control da yake zaton yana dashi sulalewa yakeyi yanayin nasa guri. "Haisaaammm" Ta sake fadi a karye kamar wadda duniya gaba daya da abinda ke cikinta suka juya masa baya. "Maimaita......don Allah" Ya fada idanunsa suna lumshewa kamar ba zasu iya sake budewa ba har abada. Muryarta da sunanta da yake kira cikin sautin yana sake kunna masa wani abune cikin kansa......yana sake buda zuciyarsa da wani irin yanayi da babu wani abu a duniya daya taba kaiwa cam qololuwar har ya budeta haka. "Haisaaammm!!" Ta sake fada da amon da yafi na dazu a nata zaton zaifi jinta. "Repeat again biftuuuuuuuuuuu" Ya fada yana sake jin qwaqwalwarsa tana haukacewa. "Hai......saaaammm" Ta kuma fada a rarrabe wannan karon saboda yadda taji azabar tana ninka ta baya idanunta face face da hawaye. "Repeat it khadeejah!!!" Ya fada da wani irin qaraji. Wani abu ya fusgi hankalinta,sai kawai ta sake tattara dukka qarfinta. "Bappiiiii!!!" Ta kira har jijiyar wuyanta tana futowa rad'a rad'a. "Nooooooo" Ya fada da sauri yana sake mata nauyinsa gaba daya. "Allahumma jannib nashshaidan.....wa jannibishshaidana ma razaqtana" Itace kalma ta qarshe daya bari ta fita a bakinsa a rarrabe yana hada haruffan da qyar suna qwace masa. *zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 08187255862 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 08187255862 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 77* _________________________ https://chat.whatsapp.com/BkfPzSEDhnsIwyCD8LNGkm?s=cl&p=a&mlu=0 *IDAN KINSAN BA ORDER DIN KAYA ZAKI DINGA SAKAWA BA* *IDAN KINSAN BA BUSINESS KIKE DA NIYYAN YI NA KAWO KAYA DAGA CHINA BA KARKI SHIGA* *_DON ALLAH KARKI BATAWA KANKI LOKACI_* *_Assalamu alaikum my loyal people_* *_Barkanmu da wannan lokaci,kuma barkanmu da warhaka_* *_akwai da dama cikin mata wadanda suke sha'awar yin order kaya daga CHINA zuwa NIGERIA,NIJER,CAMERON,CHAD da GHANA_* *_Amma rashin samun amintaccen company....ko hannun wanda zasu dinga siyan kaya ta hannunsu cikin aminci ya hanasu_* *_To a yau addu'ar da yawa daga cikinku ta amsu,don nayo muku tsarabar kamfanin da zakuyi siyayya ta hannunsu su kuma dora muku kayanku har qasarku cikin aminci ba tare da fargaba ko d'ar d'ar ba_* *_kunsan komai nawa TASTED AND TRUSTED ne,to wannan kamfanin idan akwai abinda yafi TASTED AND TRUSTED ma shine_* *_Baki da fargaba kota sisin kwabo,ni SAFIYYA HUGUMA na tabbatar da hakan_* *_Zaki iya kasancewa dasu group nasu,inda a nan zaki hadu da agent dinsu da CEO nasu gaba daya ta wannan link din,zaki samu bayanansu da komai da ya shafi mu'amala dasu_* *INA ME BAKU TABBACIN AMINCI DA INGANCI DA SAUQIN MU'AMALA DASU DA IZININ ALLAH,BAN TALLATA MUKU SU BA SAI DANA GWADA* *Allah ya dafa mana,yasa mana albarka a nemanmu,ya albarkaci halal dinmu ameen summa amee* __________________________ Duk wani qofa da bakinta zai samu daman sake magana ya tashe mata shi......duk wata dama da zata sake magana bai sake ara mata shi ba. Bai kuma d'age mata qafa ba......bai bata chance ba ko qwaya daya sai daya tabbatar ya maidata cikakkiyar MACE.....sai daya tabbatar ko ina za'aje ta amsa sunan MALLKINSA......sai da yaji a jikinsa a yanzu sunanta MATARSA......a yanzun DNA dinsa da nata sun gauraya guri daya.....kuma gaba da abadan ba abinda zai goge wannan......sai daya samu tabbacin a yanzun sunanata ta koma cikakken nasa sunan KHADEEJA MUHAMMA HAISAM ABA JIFAR......ba KHADEEJA SULTANE MUHAMMAD HAMMUD ba. Da wannan yanayin daya shiga......da wannan gushewar tunani da hankalin daya samu hakan bai sanya ya ture fahimtar samunta a matsayin CIKAKKIYAR MACE wadda bata taba mu'amala da kowanne d'a namiji ba sai shi.....da wannan ta samu alfarma ya daga mata qafa.....bayan ya tabbatar ya bude hanyarsa kaso me yawa,tamanin cikin dari. Ya mata wani irin kyakkyawan riqo yana jin kamar duk abinda yake tare dashi a jikinsa na shekara da shekaru yana sauka a hankali. Wani kyakkyawan runguma yayi mata cikin jikinsa. Ba kuka takeyi me sauti ba......amma yana jin dumin hawayenta da kuma yadda dumin dake jikin fatarsa da fatarta suke sake gogayya da juna. Duk da yadda sautin kukanta yake yankar zuciyarsa....amma a wannan gabar ya zama dole ya qyaleta tayishi. Wani irin nutsuwa.....saussauci da tarin sukuni yakeji yana lullubeshi. Wata irin cikakkiyar nutsuwa da bai taba jin irinta ba kaf duniyarshi. Virgin ce.....wani abu guda daya dake sake sanyawa yaji zuciyarsa kamar zata daskare......wani abu guda daya daya sani a wannan zamanin.....wata tsuntuwa ce me matuqar girma kima da daraja a gurin 'ya'ya maza,wanda ba kowa bane yake iya samunta ba. Bashi da wani mummunan tunani a kanta......iya tsare gidanta.....nesanta kanta da kowanne d'a namiji....izzarta da jin kanta kadai ya sani xai taimaka mata wajen tsare wannan abun....wannan ALFAHARIN KOWACCE D'IYA MACEN.....'yancinki sannan kuma TUTIYARKI.....saidai samun tabbacin da yayi a yanzun yana sake sawa yaji kamar yana sake yin balaguro ne zuwa wata duniyar ta daban. Karo na ba adadi ya dora tattausan labbansa saman goshinta ya ajiye Mata lite kiss. Yana sake jin kukanta yana sake yamutsa zuciyarsa. Ko sau daya bai bari tayi nesa da jikinsa ba tun bayan kammalar komai,ko alwala ya gaza tashi yayi duk da yasan zaman haka ba abu bane me kyau. Amma wannan nutsuwar da yake samu....mannan yanayin dake ratsa jikinsa na rungumar fatarta kai tsaye da yayi cikin fatarsa bayason ya yanke masa. Yanaso ya mata magana tun dazun amma ya kasa,zuciyarsa a narke take sosai......baisan qwalla bace cikin idanunsa sai da yaji damshinta saman eyelashes dinsa. Ya sani shi me dimbin laifi ne sosai yau a gurinta....amma inda yake godewa Allah data yarda taci gaba da kwanciya a jikinsa ba tare datayi tawaye ko bore ba,iya hakan wata qarin alfarma yakeji ta masa. A nutse ya motsata da zummar gyara mata kwanciyar yana sake jin wani sabon abu yana taso masa. Yana jin kamar sabon qarfi yake sake hadawa......amma ya yiwa kansa alqawarin a yanzu yanzu dai bazai sake tabata ba. Yanason gina komai da soyayya qauna da shauqi,bawai da tsoro ba. Tabatan da yayi da nufin gyara mata kwanciyar sai tayi yuqurin qwacewa,abinda ya fama mata can inda ya dauki zugi sosai kaman ba'a jikinta yake ba,ta furta. "Wayyo Allah na" A wahalce. Sautin ya fita da wani irin yanayi daya narkar masa da zuciya. Sai yakejin kamar da gaske yaci amanar.....sai yakejin kamar bai kyauta mata ba.....kamar he pushed too far.....duk da yasani,yayi namijin qoqari.....ya riqe kansa sosai.....yayi controlling kansa fiye da yadda ya zata zai iya,duk don ya samar mata sassauci. "I'm sorry" Ya fadi da wata murya data zama sirri ce tsakaninsa da akhnan din kawai,hannunsa saman lallausar sumarta mai santsi yana shafata a hankali da sigar lallashi. I'm sorry daya fada a yanzun,tun tana lissafa adadin nawa ya fadi sanda baya cikin hayyacinsa da yanzun daya dawo daidai har itama ta bace lissafi. This is her first time.....yasan duk yadda yakai ga lallabawa wannan ciwon wannan mikin dole ne a sameshi......wani tausayinta ne yake narkar dashi. "Biftuu?" Ya kirata da wani lallausan sauti can qasa cikin kunnenta yana sake rungumeta a jikinsa sosai. "Ka qyaleni......don Allah" "Bazan iya ba biftuu.....bazan iya ba,not now......kiyi haquri kinji?" Ya fada yana yaye gashin kanta da tun dazu yake rufe mata fuska. Fuskarta da idanunta kadai yake so ya gani,koda ya siririn hasken da yake dakinne. Yana jin gaba daya ragamar rayuwarsa da duniyarsa yanzu haka a tafin hannunta Wani mahaukacin so cakude da kishinta ke sabauta kowacce gaba ta jikinsa. Sai a yanzun a wadannan tsukin ya fahimci ma'anar rayuwa. Sai a yanzu yasan yana rayuwa.....a baya rayuwa kawai yake da sunan rayuwar bana haqiqa ba. "Idan na barki.....mutuwa zanyi my princess" Ya fadi da kaman yaron goye da wani irin yanayi na tausayi yana kwantar da kansa saman nata kan. "Kiyi kuka yadda kikeso indai zuciyarki zata daina zafi.....na miki ba daidai ba,kuma na cancanci hukunci Idanunta ta lumshe tana jin bugun da zuciyarsa keyi kaman zata balla qirjinsa. Tunda ta samu kyakkyawan masauki cikin qirjinsa abinda take saurara kenan. Kukanta na kunya ne.....matsananciyar kunyar da batasan inda zata kaita ba. Itace yau da hada jiki da sheikh muhammad haisam......yau itace wani d'a namiji yayi zurfi a sirrinta irin zurfin da ko ita bata isa tayishi ba?. Yau ta raba sirrinta mafi girma da sheikh muhammad haisam.....ya mallaka mata wani abu da tayi imanin itace mace ta farko data fara sani.....data fara gani.....data fara ji a tattare dashi. Kunya takeji.....kunya takeji kamar ta kasheta. Tabbas qafafunta cinyoyinta qirjinta da bayanta duka zugi suke mata.......saidai abun baikai yadda ta zata ba.....abun baikai tsanin yadda ta hangeshi a tattare da falaak ba. Akwai wani taushi cikin halayyarsa......akwai wata nutsuwa data tabbatar BAIWA ce Allah yayi masa. A kowanne yanayi nasa sai ya nuna DATTAKO,sannan kuma KAMALARSA tana sake nuna kanta. Ta tabbatar akwai banbanci tsakanin abinda ya faru da ita da kuma wanda ya faru da falaak nesa ba kusa ba. Duk da can cikinta tana jin wani irin yanayi mara dadi da ko motsawa batason yi,numfashinta tana jinsa a qirjinta,gabbanta dukka amsawa suke har yanzun,amma ta tabbatar baiyi mata yadda take zata ba. Saidai yadda komai yake baqo a gurinta ya sanya takejinta wani iri. Tana kuma sake jin kunya tana binneta idan ta tuna a yadda ya ganta a dazun,da kuma yadda take kwance yanzu haka cikin jikinsa "Kiyi haquri....." Ya sake fada yana narke mata har ya sanya ta sake shigewa jikinsa ba tare data shirya ba,shi kuma ya sake bata dama sosai,saidai da sauri ta sake qoqarin janyewa amma abun dazu na radadi da zugin da takeji ya sake sokarta "Wayyo Allah na" Ta sake fadi da muryar kukan nan. "Ya salammm.......I'm sorry" Ya sake maimaitawa a rude yana qoqarin supporting bayanta da hannunsa. Ido ta lumshe,ragowar hawayen data riqe yana gangarowa,ya sauka a hankali ta tsakanin lallausar gargasar qirjinsa ta ratsa fatarsa. Ya lumshe idonsa yana jin dumin hawayen yana gauraya da d'umin jikinsa da ya soma hada wani sabon zazzabin. Tasha ji.....tasha karantawa,kalmar KIYI HAQURI wata kalma ce da maza suka dauketa da girman gaske. Wata kalma ce da take musu tsada,wata kalma ce da suka kambamata,furtawa mace ita a gurinsu faduwa ce...zubewa ce,amma sai gashi,a gareta ba haka abun yake ba. Yana da sauqin ce mata KIYI HAQURI,ba kuma iya na yau ba....ba iya na yanzun ba kawai,tun a baya. Zata masa adalci dari bisa dari a nan gurin....zata bashi dukkan lambar girmamawa da kuma lambar yabo ta sanin KIMA NA DIYA MACE. (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) Idanunsa ya dora saman qaramin agogon dake jikin bedside lamp din,sai ya nuna masa qarfe uku na dare,awa biyu kawai zuwa da rabi ya rage ayi sallar asuba. Cikin nutsuwa da dabara ya janyeta a jikinsa,ya maida gurbinsa da duvet din da dukkaninsu dama pillows din suka watse a qasan gadon,sannan ya sauka a hankali yana wucewa zuwa bathroom din. Tsaiwa kawai yayi gaban mirror yana duban kansa. Wani qawataccen murmushi ne kawai ya subuce masa,yayi qasa da kansa yana juya komai yadda ya wakana. Shi kansa mamakin kansa da kansa yakeyi,duk da yasha 'yar wahala shi kansa kafin ya gano hanyarsa,hanyar daya tabbatar bai gama budeta gaba daya ba....to amma yaji abinda baki da kwatance basu taba kwatantowa gauraye daidai ba. Ya tuna kalmar maleek a wancan ranar. "Ashe mun dade a matsayin buhunbuna kuma bahuna ba tare da mun sani ba?" Murmushi ya sake subuce masa sanda ya sakarwa kansa ruwa a cikin shower Maleek baiyi qarya ba,amma kuma sunfi bahuna ma.....saidai yace sun jima cikin farfadiyar rayuwa.....sun dade da zama kwalaye da gwangwanaye marasa amfani,sai yanzu da suka yiwa kansu babban gata. Shi daya cikin shower din,ruwa yana ratsashi yana tunani. Lallai ashe iyayensu sunso musu rahama.....iyayensu sunso musu alkhairi da sukaso suyi aure tun kafin yanzu. "In sha Allah,zan aurar da d'ana ko 'yata tun suna da qananun shekaru" Ya furta can qasan ransa a hankali yana yin baya da tattausar sumarsa da ruwa ya sanya ta kwanto ta gaban goshinsa. Har ya gama shiryawa cikin wata tattausar riga cotton me kama da Moroccan thobe bata ko motsa ba. Idanunsa da hankalinsa gaba daya a kanta,ba wani minti da zai shude ba tare daya aza idanunsa a kanta ba. A cikin jinin jikinsa a yanzu yake jinta.....cikin kowanne bugawa ta zuciyarsa da fitar numfashinsa. Wata madaukakiyar daraja....martaba da kima tata take ninkuwa cikin ransa. Wani matsanancin tausayi da qauna me narka zuciya. A ransa yakejin zaiyi komai saboda ita....zai iya aikata saboda ita. A baya.....saboda SULTANE ne kawai......amma a yanzun........zaiyi komai SABODA ita.....zaiyi komai saboda ta cancanta,zai aikata komai saboda ita din tasa ce....mallakinsa ce.....kayansa ce ita!. A baya saboda ETHIOPIA........amma a yanzun yana jin tilas mammina ta karbi hukunci a kurkusa. Saboda KHADEEJA.....saboda BIFTUU.......saboda AKHNAN......saboda matar SHIEKH MUHAMMAD HAUSAM ALSAAMIT (the silence one). A nutse ya tako inda take kwance,yana qishirwar ganin fuskarta,wannan blue eyes din.....har wannan hawayen nata da suke qarawa eyelashes dinta wani mugun kyau. Amma ya sani duka a yanzun ba abu bane me yiwuwa. Zai taro match ne kawai. "My princess" Ya furta haruffan sunan da wani irin girmamawa. Ta jishi....taji zamansa kuma dab da ita,taji yadda ya kiratan da wani yanayi na GIRMA,amma kunya ba zata barta ta motsa ba. "Biftuu" Shuru. "Akhnan" Shuru. "Khadeeeeeejaaaah!" Wannan karon kasa daurewa tayi sai data runtse idanunta tana jin yadda tsigar jikinta ta yamutsa. Yaga alamun saqon ya isa. Yaga reaction nata,saidai shi kansa yasan tayi qoqari da bata nuna ba. Sai ya sanya yatsunsa yana yaye bargon iya kanta,ya sunkuyo daidai fuskarta,abinda ya sanya sauran ruwan dake kansa ya diga mata d'is gefan fuskarta. Ta runtse idonta,ya saka yatsansa yana dauke ruwan. "Kaina bisa wuyana.....afuwa nake nema" Ya fada da wani irin laushi,kamar ba shine wannan jarumin ba.....zakin hukumar binciken manyan laifuka na sirri na farin kaya. Kamar ba shine wannan zakin ba......dake iya bibiyar laifi dame aikatashi komai girmansa ba komai tsanani da girman laifin. "Zan baki guri idan kin zabi shiryawa da kanki,amma idan nakai qofa baki tashi ba.....na samu ticket na taimaka miki da kaina" Ya fadi yana miqewa,ya kuma ja da baya sannan ya fara takawa. *zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 08187255862 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 08187255862 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 78* _________________________ https://chat.whatsapp.com/BkfPzSEDhnsIwyCD8LNGkm?s=cl&p=a&mlu=0 *IDAN KINSAN BA ORDER DIN KAYA ZAKI DINGA SAKAWA BA* *IDAN KINSAN BA BUSINESS KIKE DA NIYYAN YI NA KAWO KAYA DAGA CHINA BA KARKI SHIGA* *_DON ALLAH KARKI BATAWA KANKI LOKACI_* *_Assalamu alaikum my loyal people_* *_Barkanmu da wannan lokaci,kuma barkanmu da warhaka_* *_akwai da dama cikin mata wadanda suke sha'awar yin order kaya daga CHINA zuwa NIGERIA,NIJER,CAMERON,CHAD da GHANA_* *_Amma rashin samun amintaccen company....ko hannun wanda zasu dinga siyan kaya ta hannunsu cikin aminci ya hanasu_* *_To a yau addu'ar da yawa daga cikinku ta amsu,don nayo muku tsarabar kamfanin da zakuyi siyayya ta hannunsu su kuma dora muku kayanku har qasarku cikin aminci ba tare da fargaba ko d'ar d'ar ba_* *_kunsan komai nawa TASTED AND TRUSTED ne,to wannan kamfanin idan akwai abinda yafi TASTED AND TRUSTED ma shine_* *_Baki da fargaba kota sisin kwabo,ni SAFIYYA HUGUMA na tabbatar da hakan_* *_Zaki iya kasancewa dasu group nasu,inda a nan zaki hadu da agent dinsu da CEO nasu gaba daya ta wannan link din,zaki samu bayanansu da komai da ya shafi mu'amala dasu_* *INA ME BAKU TABBACIN AMINCI DA INGANCI DA SAUQIN MU'AMALA DASU DA IZININ ALLAH,BAN TALLATA MUKU SU BA SAI DANA GWADA* *Allah ya dafa mana,yasa mana albarka a nemanmu,ya albarkaci halal dinmu ameen summa amee* __________________________ Firgigit tayi,ta miqe ta zauna,saidai tun a zaman ta gane shayi ruwa ne,amma sai ta kanne ta fara yunqurin sauka daga gadon. "Wayyo bappi" Kalman ta subuce daga bakinta. Abinda ya sanya haisam tsaiwa cak kenan,sannan ya waiwayo a hankali,sai kuma ya juyo gaba daya yana dawowa cikin dakin. Ba dama ta biyu....ba shawara.....ba kuma dogon tunani ya dauketa cak kamar jaririya,kai tsaye kuma ya wuce bandakin da ita ba tare daya kula da magiya da qananun koke kokenta ba,wanda ya tabbatar tanaso ya sauketa ne,bataso ya sake ganin jikinta a karo na biyu. ★★★Lallausar black slim fit shirt ce a jikinsa me dogon hannu wadda ya nannade hannunta ya barshi iya gwiwar hannun nasa,akwai dan rubutu kadan daga qasan rigar gefan dama da wani gold zare wanda ke dauke da sunan brand na rigar (zegna). Three quarter ne a jikinsa shima baqi wanda duka kalolin suka cakude suka fidda wannan sassanyar farar kalar fatar tasa. Yammaci ne.....wanda ya dauki awanni daga abinda ya faru tsakaninsu daga daren jiya zuwa yau. A wannan yammacin,tarin saqonnin da suke fitowa daga sassan nanay zuwa wannan sashen ko daya bai samu isowa garesu ba. Hadimai da dukka 'yan aikin dake da alhakin kula da sashen a yau sun samu iyaka da sashen,iyakar dasu kansu basu san dalilinta ba. Shi kadai.....daga shi sai ita ne cikin yinin gaba daya a sassan. Ya lullubeta da wata irin soyayya. Ta rikitashi gaba daya,saboda yinin da tayi tana share hawaye. Yana ankare da ita,abinda ya hanashi dukkan wani sukuni kenan. Ya sani rigima ce daban takeji kuma,saboda taso ya qyaleta ta kula da kanta,wani abu da shi kuma sam bazai iya ba. Daidai da space da takeso ya bata ya hana mata,ya wuni sir da ita,koda sallolinsa na azahar da la'asar dukka a nan sukayi jam'i ita dashi. Koda bata gaya masa ba yasan gurin a yanzu ya daina wannan zugin da zafin,don da kansa ya dinga hada mata wani ruwan zafi daya sanya wasu abubuwa da batasan meye ba,wadanda suka sanyaya mata gurin sosai. Har tayi bacci,baccin da ko sanda ta tashi ta sameshi zaune a gefanta riqe da littafi yana dubawa. Yinin ranar waya kawai yake dagawa,duk motsin da zatayi idaninsa akai. So yake ta kalleshi,amma ya rasa dalilin daya sanya taqi kallonsa kwata kwata. Yayi dukkan qoqarinsa amma ko sau daya taqi yarda ta kalleshi. Kaman yanzu da yake takowa dauke da wani irin baqar butar shayi,wadda ta dace da shigar jikinsa. Ta saci kallonsa tana ganin yana mata wani irin kyau a idanu da zuciyarta,ya koma mata tamkar BUZU tamkar dan qabilarta. Cikin sa'a ya kamata,ya kamata da wadannan idanun nasa,ya kalli tsakiyar blue eyes dinnan nata da yaketa shauqin kalla. Abinda ya gani a cikinsu kuma yaso birkita nutsuwar da yaketa qoqarin samu tun bayan da akayi sallar asuba. Bayan sallar asubar komai ya zame masa sabo. Bayan sallar asuba sai yaji duk duniya ba abinda yake buqata irin ya sake jinsa cikin jikinta. A wannan lokacin,ya yiwa zuciyarsa da gangar jikinsa wani irin qarfa qarfa,sai kawai ya buge da karatun da dole ya dakusar da abinda yakeji,don a sannan yana zaune a gabanta yana gadinta ne. To amma a yanzun data kalleshi......a yanzun da take sanye da wata gown dark Olive color,silk material da yake shaking yake kuma kwanciya a jikinta,sai yakejin kamar haqurinsa zai iya gazawa. Zama yayi sosai a gabanta da butar shayinsa. Ya tanqwashe qafafunsa kamar yadda qaramin yaro yakeyi a sanda ake koya masa ladabin zaman cin abinci. Qoqarin lalubar qwayar idanunta yakeyi amma ta hanashi hakan. Ya narke fuska yana jin yadda take sake janye hankalinsa,yana kuma jin yadda take sake fusgar feelings dinsa xuwa gareta. "Hey" Ya fadi a nutse da wani sassauqan sauti. Yadda ya kiratan,tasan ta yiwa kanta qarya idan tace zata iya jurewa bata juya ta kalleshi ba. Batasan da wanne siddabaru yake amfani ba.....a qa'ida ya kamata ta tsaneshi......ya kamata taji haushinsa.....ya kamata ya fita daga ranta saboda ya keta haddi da iyakar da ba'a taba keta mata ba. Amma haka kawai sai takejin wata irin mahaukaciyar soyayyarsa tana hudata. Ko na minti biyar ya matsa daga inda take,sai taji kaman ya mata nisa ne na shekara biyar. Yadda ya tsareta da idanu ya sanya hawaye taruwa mata a idanu. Haisam ya lumshe idanunsa tare da budesu lokaci daya,wannan feelings din yana sake fadada cikin jikinsa. "Shshshshsh.....it's okay" Ya fadi da muryar rada sosai wanda koda kana dab dasu ba lallai kaji ba. "Look at me" Ya sake fadi yana lalubar qwayar idanunta bayan ya kamo tafukan hannayenta ya riqe cikin nasa. Kai ta girgiza,ta yaya zata iya kallonsa yadda yace?. Qasa sosai yayi da muryarsa,still bai daina kallonta ba. "I'm here my healer" Ya fadi da harshen faransanci. Da wannan accent din.....da wannan yanayin dake dimautata "My healer?.....har ya warke kenan tunda ya mata mugunta jiya?" Ta tambayi kanta tana lumshe idanunta gami da budesu lokaci daya. Sunan taji ya sauka a ranta da wani irin girman matsayi. "Giiftii" Ya fada softly. Ta sani,yaudararta yakeso yayi ta juyo ta kalleshi,ita kuma ba zatayi ba. (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) "Zaki dan qaramin.....don Allah" Ba tare data shirya ba ta waiwayo da hanzarinta. Murmushi me kama da dariya ya kubce masa. Sai a sannan ta fahimceshi yaudararta yakeso yayi,ya tsoratata kenan,don butar shayin gabansa ya nuna mata. "Wannan.....shi zaki qaramin" Harararsa takeso tayi kaman yadda takewa su sheshnaz,saidai shi kuma ya mata girma da nauyi ta masa hakan,saita dauke kanta kawai. "Giiftii" Ya sake kiranta da accent na Oromo. "Zazzabi nake.....da gaske,amanar nanay tana hannunki,ya cancanci na kwanta....ki kula dani" Zuciyarta tadan motsa kadan,a dazu ta yarda tea din yake nufin ta dada masa,amma a yanzu sai taji cikin ma'anar zancansa kamar ba akan kulawa normal yake magana ba. Kafin shi ko ita wani ya sake cewa komai wayarsa dake cikin jerin security na gidan tayi haske. A kasalance,kamar bazai daga ba ya latsa,muryar ta fito tar ta ciki. "Mama oromo ta qaraso babban parlor na fuskar yamma". "Okay" Ya fada a taqaice yana yanke saqon. A nutse ya tattara idanunsa dukka akan fuskar akhnan yana kallonta. "Nanay tazo.....tazo dubamu" Ya fadi da wani coolness. A dan tsorace ta daga idanunta tana dubansa,sai taba shi zaune yake hankalinsa kwance yana kallonta da wannan narkakkun idanun nasa dake razanata. Dukka idanunta ta fiddo waje tana dubansa,a hankali yaga yadda idanun nata suka fara tara hawaye. "Nanay.......kaine?" Kai ya girgiza da sauri. "Bani na kirata ba.....nasan dama zata shigo dole,zata dubani,zatabi ba'asin aiken da tayo". Sosai taji hankalinta ya tashi,ba nanay ba.....a yau dai ko noorah batajin zata iya kalla ballantana nanay da kanta. Kai koda birra ma,gani take duk wanda ya kalli qwayar idanunta zaiga komai,zaiga komai daya faru tsakaninta dashi a tsakiyar daren jiya. Qasa tayi da kanta tana qoqarin boye hawayenta. "Giiftii" Ya kirata a tausashe. Hannunsa ya miqa mata sanda ta daga kan nata,da idanunsa kuma ya mata alama data dora masa nata hannun. Bata musa ba,ta dora din. "Kalleni" Ya sake fada yana dubanta sosai. Sau uku tana attempting hakan tana kasawa,sai ana hudun ta samu ta iya tsaida dubanta a kan nasa. "I'm here with you.....im not going anywhere" "Tsoro nakeji.....kada nanay ta gane" Dariya yakeso yayi,dariya sosai na irin quruciyar akhnan din. Komai nata yana sake nuna masa irin qarancin shekarun da take dashi,komai nata yana sake nuna masa bata da wani experience na rayuwa,an karkata tunaninta ne kawai akan izzarta mulkinta sarauta da kamfaninta. "You're safe" Ya fada a taqaice,saidai yadda take kallonsa ne kamar bata gamsu ba,har sai daya sake maimaitawa. "......With me.....you're safe,ba wani abu da zan bari ya sameki..." Kanta ta gyada a hankali,ya miqe tare da ita yana fadin. "Ki komai normal yadda kika saba....karki wani abu da nanay zata dauka naci amanarta ne...." Ya fadi da guntun murmushi. Waiwayawa tayi idanu a narke tana kallonsa,kallon data masan wanda ya masa kyau ainun,ya danne dariyarsa,wasu hawayen suna taruwa. "Kaine ka jawomin.....kuma saina gaya mata k......" "......kin kwanta da mijinki a darenku na farko?" Ya qarashe mata maganan yana katse mata numfashi gami da dage mata dukka girarsa. Wata irin kunya me bala'in nauyi ta taso ya danneta,ta rasa inda zata boye fuskarta taji dadi,sai kawai ta sake masa kuka,shi kuma ya bude mata dukka qirjinsa yana rungumeta,damar da yake jira kenan dama ya samu. Tun asuba yake neman dalilin rungumeta amma bai samu ba,a yanzun daya samu damar sai ya mata kyakkyawan riqon da ya tayar masa da duk wani tsumi na jikinsa,ya dinga sauke boyayyen numfashi yana kuma lallashinta a hankali cikin dabara tare da sake mannata a jikinsa sosai idanunsa suna lumshewa tare da budewa duka lokaci guda. *zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 08187255862 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 08187255862 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 79* ________________________ *_Amintaccen gurin siyayya_* *_ingantattun kaya akan ingantaccen farashin da ba irinsa a kasuwa_* *_BONONZA DA PROMO akai akai_* *dukka sai a HUGUMA CLOSET* *Duniyar kayan yara,mata,maza,dukka* *shaddodi,atamfofi,laces,abayas,jakankuna,takalma,agogo,sarqoqi,English wears,night wears,under wears,da duk wani nau'in sutura babba da qarami* *_Karki yadda ayi babu ke.....leqa kiga yadda closet din HUGUMA kullum ke cike da kaya akan farashi me kama da KYAUTA_* *_YAN SARI....YAN REPOSTING.....DA SARAKAN ADO MASU SIYA DON KANSU....DUKKA INA MUKU MARABA_*🤝🤝🤝🤝 https://chat.whatsapp.com/FrqgC0YmUWP4FPmUzYuLJX _________________________ "Tu es détendue?(“Are you feeling relaxed now?)" Ya fada yana hada sautinsa da qyar cikin maqoshinsa saboda yadda yaji komai yana son sake kwance masa,kamar ma baiyi komai ba,kamar yanzunne yake buqatar yayi komai. Accent din nan nasa da yaren French ya shiga kunnenta da wani irin sanyi da laushi. Bata sani ba,ko Allah ne yake kamata?.....ko Allah ne yake mata hukunci akan gatsalinta?. Ta masa gorin yaren French,duk da cikin zuciyarta ne amma a yanzun bayan daya tabbata ko ya iya,da wata irin qwarewa da ko ita da yake yaren qasarta. Ko ita da yake yare na biyu a gurinta bata kaishi iyawa ba,sai ya zame mata wani irin jarrabi. A duk sanda zaiyi yaren,yana shigewa ta narke ta cikin kunnuwanta,ta kuma kwarara har cikin zuciyarta. Janye jikinta baya tayi kadan,sai bai hanata ba,saidai kaman yadda taga ya koya,wani irin mayen kallo da yafi na baya,wani irin kallo da shanyayyu kuma narkakkun idanuwasa dinnan dake mata wani irin tsananin kwarjini. Ba'a komai yake bude baki ya mata magana ba,yafi amfani da body language a komai nasa sama da magana,kamar tana masa wahala wani lokaci ko bakin nasa yana masa ciwo. Ko yanzu ma hannunsa kawai ya miqa mata bayan ya tabbatar ta lullube jikinta da wata lafiyayyar silk abaya me tsananin daraja,wadda daga gefenta a bayanta yake dauke da wasu qananun stone da aka rubuta haruffan sunanta cikakke dasu. Iya wannan dutsen.....iya shi kadai idan aka cire kudinsa dabanne,iya shi kadai idan aka kankare kudine ba abayar kawai ba. Yana cikin nau'ikan duwatsu masu daraja a duniya da kamfanin suka sarrafa suka fidda adon sunanta. Zasu yiwa sheikh muhammad haisam komai,saboda ya cancanta,yana da wata irin kima da daraha me yawa a gurinsu. Lallausan tafin hannunta ta saka a nasa,ya runtsesu a hankali cikin zara zaran yatsunsa sannan suka fara takawa zuwa parlor din yana bude duk qofar da suka iso gareta. Tana daga gefan nanay daga qasa,hannunta rungume da ledar turaren da tunda nanay ta miqa mata qamshinsa yake dukan hancinta. Turaren kamfanin shuwa ne,shuwa incense and more(turarukanta duniya ne,seriously jiya dana qona wani a parlour na......ya Allah🥰,irin qamshin nan da idan ka shiga daki ba zakaso ka fita ba,irin asalin qamshin turarukan wuta ba na yanzu gamje gamje ba,trust me akan kowanne turarukan wuta da zan recommending muku a novel dina +234 704 229 3387). Banda kiran sunan Allah da take tsakanin jiya zuwa yau,ba abinda zai hanata kwanciya magashiyyan,saidai kuma tana gayawa kanta tana sake maimaitawa,qwarin gwiwa takeso......qwarin gwiwa take buqata,bata buqatar ta kwanta yanzu. Abu mafi gigitata ta daga mata hankali shine.....wannan izzar da take gani tattare da ita......wannan izzar wadda take sanyawa bata sanin da zamanka a guri ballantana motsinka.....wannan izzar da motsinta ma kawai yake zame mata abun kallo. A jiya zuwa yau din wani sashe me girma na zuciyarta yana magana da ita......yana kuma gargadinta. "Ki janye saamee.....zaki iya kuwa?,ba wata hanya......ba kuma wata fuska ko daya da zaki samu shimfida shirinki. Da mutum me shuru,da mutum me izza kowanne shiri wahalar isa ga manufa yakeyi" Take maimaita mata,amma ko sau daya taqi bawa wannan tunanin hadin kai. Daga nesa ta hango nanay..... Kallo d'aya tal tayi mata amma sai takejin kamar nanay din na kallon komai a jikinta. Tadan so taja tunga amma ya matsa hannunta kadan. "Relax please" Ya fadi yana motsa wadannan kyawawan labban nasa. "Kowanne action naki yana determining abinda kika boye.....she's not the Allahn musuru......ba abinda zata fahimta" Ya sake fada softly yana qara yiwa hannunta kyakkyawan riqo. Waya nanay din takeyi,kuma batakai ga ganin fitowarsu ba sai da suka iso tsakiyan parlor din. Tayi sallama da wanda take wayar tana ajeta gefe idanunta a kansu fuskarta dauke da murmushi. Cikin yanayi na girmamawar nan tata,cikin yanayi na nuna zallar qaunarta ga wadannan halittu guda biyu ta miqe,idanunta a kansu,tana gaza gane wanda tafi qauna tsakanin ita ko shi?. "Ina maraba da d'iyata" Nanay ta furta tana budewa Akhnan hannuwanta. Wani irin kunya,wani irin nauyi suka taso suka lullubeta,ta yaya zata fara shiga jikin nanay bayan duk abinda suka aikata ita da dan nata?. Salon taji wani abu?,salon ta gane komai?,maimakon ta shige jikin nata bayan ta zame hannunta daga cikin na haisam din,saita tako a hankali ta iso gaban nanay din ta tsugunna tana gaidata cikin takatsantsan da ciwonta. Durqusawa nanay din tayi tana murmushi ta dagota tana sanyata cikin jikin nata. (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) "Yaushe muka fara surukuta dake?" Ta tambayeta tana murmushi,saidai kuma hancinta ya jiyo mata sauyin wani qamshi cikin jikinta,kamar yadda taji dumin jikin Akhnan din ya qaru kadan,abinda ya d'arsa wani zargi kadan a ranta,saita janye Akhnan din baya kadan tana duban Fuskarta. "Ina fatan kin tashi lafiya" Nanay ta sake fadi tana karantar wani haske da taga fuskar Akhnan din tayi. Ta washe da wani irin yanayi da yaso sake qarfafa zarginta a ranta,tana jin wani nauyi na duban haisam da take jinsa a tsaye a gefansu. "Lafiya alhamdulillah nanay" Ta amsa mata tana jin duk duniya idan zasu hadu ba zata iya hada idanu da ita ba. "Na yita aike......ba alamun samun amsa,har na dan tsorata na dauka yanayin jikin nasa ne.....nayita kiran wayoyinku duka ba wanda na samu" Ta qarashe maganan wannan karon kai tsaye tana aza dubanta akan haisam. Karon farko da yaji wani nauyi na kallon idanun nanay.....a yau din sai yaji kallo dama idanuwan nanay din kamar daban suke da kallonta na baya. Tunda ta qarashe maganan idanun cikin nasa.....hakan yana gaya masa shi takeso ya amsa mata tambayar bawai diyartata ba. Shidai wayarsa baisan inda ya jefata ba,tun daga sanda suke magana da omar maganar da har yanzu ba'a kammalata ba,har zuwa yanzu bazaice ga inda take ba. Tata wayar ma bai ganta ba ballantana ya fadi inda take. Samun kansa ya kawai da aza hannunsa saman sumarsa yana shafawa,ya sake taku biyu yana qarasowa gaban nanay din,da wani yanayi daya sanya Akhnan satar kallonsa ta qasan idanu sanda yake gaida nanay din. "Da gaske ne" Ta fadi a ranta,da gaske shi din shagwababben nanay dinne......da gaske ne shalelenta ne,kusanci qauna da shaquwar da take gani a tsakaninsu yana sanya mata wani shauqi.....yana sanya mata burin cewa Dama tata MAHAIFIYAR tana raye,yana saka mata jin dama haka rayuwa tsakanin uwa da d'a take?......me yasa wannan qaunar me zurfi......wannan yanayin gaba daya bata ganinsa tattare da MAMMINA?. Ta nuna mata kulawa a komai nata.....amma wannan kallon....wannan shauqin da take gani cikin idanun nanay zuwa ga haisam ita bata taba ganinsa tattare da mammina ba. "Me yasa?" Ta yiwa kanta tambayar da kafin ta tsaya laluben sharhi ko amsarta muryar nanay ta ratsa kunnenta. "Zuna diyata". Idanunta ta dawo dashi kansu,sai taga ya zauna shi. Ya zauna kusa da nanay kamar qaramin yaro,saitin qafafuwanta irin zaman da hadimai keyi gabam shugabansu. A hankali ta zauna,yanayi daya sanya Nanay sake kallonta sosai tana qara jin zargi cikin ranta. Dauke kanta tayi a hankali,tana jin wani abu cikin ranta,wani abu me kama da nauyi. Inde abinda take zato ne yayi.....indai zarginta ya tabbata da gaske.....lallai ya shayar da ita mamaki kaman yadda motii keta mata dariya tun jiya. "Balqees taso kuyi sallama.....komawar gaggawa ta sameta....amma bata sameku ba" Ta qara magana taka duban Akhnan. To me zatace?,bata data cewa,hasalima yadda nanay ke kallonta a yanzun gani take kawai ta dago komai. Sam batasan ya hana shiga da fita ba kwata kwata a sassan. "Barka da warhaka obbo" Saamee tayi namijin qoqarin fada tana danne abinda yake taso mata. "Barka kade" Ya amsa mata saidai idanunsa akan Akhnan wadda ke murza yatsunta da wani irin yanayi na rashin sakewa. Yawu ta hadiye da qyar,karon farko data taba ganin tozarci irin wannan. Me gaisuwa daban,wanda ake kalla a amsa gaisuwa daban. "Ya jikin naka?,nayita zuwa don na duba lafiyarku da abincinka......amma sun sanarmin,....." "Ba maijin yunwa a cikinmu.....banason dogon hayaniya saboda zazzabi na tashi,shi yasa na bada wannan umarnin" Ya bata amsa wannan karon yana maida dubansa kanta. Maganganunta kawai ji yake suna katse masa jin dadinsa,yana jin kamar suna masa shishshigi ne dason hanashi morewa satar kallon Akhnan,wadda suke magana qasa qasa ita da nanay ba tare kuma da yasan me suke cewa ba. A yanayinsa.....taga amsawar tasa batayi daidai da maganarta ba. Kamar dai wanda akewa dole. Anya zata iya?,anya ba zata canza salo ba?. Ta dan lumshe idanunta tana tuna wani abu guda daya da yake tattark hankalinsu a kanta. Rashin lafiya.....inde zata kwanta bata da lafiya zata samu dukkan tattali da kulawa.......inde tana jinya cikinsu ba wanda hankalinsa baya kaiwa kanta. Ba zata kwanta ba kuwa?. Cak tunaninta ya tsaya akan wannan shawarar,saita zame kyakkyawan jakar ledar turaren daga cinyarta tana ajiyewa gefe,abinda yadan dauki hankalin nanay kenan. "Lafiya?" Ta tambayeta ganin tana shirin tashi. "Kaina yake dan ciwo kadan kadan,zanje nasha maganina ne" Shuru nanay tayi tana dan dubanta. "Amma kin shanye wadancan magungunan kuwa?" Qasa tayi da kanta tana murza yatsunta,irin wannan kulawar take buqata daga gurin kowa,wannan kulawar takeso ta yiwa nanay jagora wajen sanyashi fuskantarta da nufi na aure. *zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 08187255862 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 08187255862 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 80* _________________________ https://chat.whatsapp.com/BkfPzSEDhnsIwyCD8LNGkm?s=cl&p=a&mlu=0 *IDAN KINSAN BA ORDER DIN KAYA ZAKI DINGA SAKAWA BA* *IDAN KINSAN BA BUSINESS KIKE DA NIYYAN YI NA KAWO KAYA DAGA CHINA BA KARKI SHIGA* *_DON ALLAH KARKI BATAWA KANKI LOKACI_* *_Assalamu alaikum my loyal people_* *_Barkanmu da wannan lokaci,kuma barkanmu da warhaka_* *_akwai da dama cikin mata wadanda suke sha'awar yin order kaya daga CHINA zuwa NIGERIA,NIJER,CAMERON,CHAD da GHANA_* *_Amma rashin samun amintaccen company....ko hannun wanda zasu dinga siyan kaya ta hannunsu cikin aminci ya hanasu_* *_To a yau addu'ar da yawa daga cikinku ta amsu,don nayo muku tsarabar kamfanin da zakuyi siyayya ta hannunsu su kuma dora muku kayanku har qasarku cikin aminci ba tare da fargaba ko d'ar d'ar ba_* *_kunsan komai nawa TASTED AND TRUSTED ne,to wannan kamfanin idan akwai abinda yafi TASTED AND TRUSTED ma shine_* *_Baki da fargaba kota sisin kwabo,ni SAFIYYA HUGUMA na tabbatar da hakan_* *_Zaki iya kasancewa dasu group nasu,inda a nan zaki hadu da agent dinsu da CEO nasu gaba daya ta wannan link din,zaki samu bayanansu da komai da ya shafi mu'amala dasu_* *INA ME BAKU TABBACIN AMINCI DA INGANCI DA SAUQIN MU'AMALA DASU DA IZININ ALLAH,BAN TALLATA MUKU SU BA SAI DANA GWADA* *Allah ya dafa mana,yasa mana albarka a nemanmu,ya albarkaci halal dinmu ameen summa amee* ___________________________ "Saura kadan" Kai ta gyada. "Ki kammala shanyeshi,indai har jikin bai sauqi ba wannan karon asibiti kawai ya kamata ki fita gaba daya" Ta fada kulawa. "To in sha Allah.....na gode" Ta fadi tana rusunawa sannan ta fara takawa tana fita a gurin. Kunnuwanta da zuciyarta cike da burin ko sau daya yace. "Allah ya baki lafiya.....sannu.....ki kula da kanki....kisha maganinki.....ki.kwanta ki huta.....ki rage damuwa" Saidai a maimakon hakan ma,a daidai wannan lokacin idanunsa suna kan Akhnan din. Maido idanunta nanay tayi kansu,sukayi kyakkyawan gani,yadda ya nutsu ya tattara hankalinsa dukka akan motsinta. Yakai hannunsa don gyara mata gashinta daya sauka gefen fuskanta,sai ya janye da sauri jin motsin nanay din. Itama basarwa tayi,tayi kamar bata gani ba.....tayi gyaran murya tana cewa. "Ga turare daga balqees,satin gaba zata dawo.....nima wucewa zanyi yau din ina da baqi......" Ta furta tana miqewa. A hankali Akhnan din ta miqe,cikin ranta tana jin Kamar ta bita. "Jikin naka kamar yayi kyau......" Ta fada tana dubansa cikin tsakiyar idanunsa. Ya sani.....yasan nanay dinsa,ya santa sarai wajen saurin gano abubuwa,yana jin nauyin kallon da take masa sosai,to amma bazai bari ta sake rabashi da ita ba sam,bazai dauka ba. A yanzun bayajin akwai wani abu da zai bari ya shiga tsakaninsa da ita har abada. "Da sauran zazzabin nanay" Ya fada da wannan yanayin da zuwa yanzu Akhnan ta saba ganinsa tattare dashi. Yanayin nan na narkewa.....sangarta da shagwabewa nanay din. Da gaske kaman yadda ta gaya mata ne.....yana komawa tamkar wani qaramin yaro ne wanda baida kowa sai mahaifiyarsa. Idanunta ta janye.....can qasan ranta tanaso ta tafi da Akhnan ne.....tanason ta cika kwanakin da sauran abinda ta tanadar mata,tana tsoron wannan kallon da take gani akan yarinyar cikin idanunsa,amma haka kawai saita kasa cewa komai,ta rufe da fadin "Allah ya qara lafiya" Dan qaramin qayataccen murmushi ya subuce masa. "Babu kamar nanay" Ya fada can qasan ransa yana jin wani abu yana ratsashi,amma a fili sai yace. "Ameen,na gode,Allah ya qara girma,zan kawota da kaina zuwa goben idan na samu sauqi". Dan tsaiwa nanay din tayi,tana jin maganan nasa kamar ba asalin saqon dake cikin maganar take isarwa ba. Shima ya lura da hakan,da sauri ya koma zuwa ga kalaman daya furzar a yanzun,sai ya tsinci wani dan nauyi kadan a cikinsu. Tattaki suka fara mata shi da Akhnan din,saidai suna zuwa qofar qarshe yasa hannu ya jawo Akhnan din baya a tausashe nanay ta qarasa fita. Hannu ya sanya ya maida key din qofar ya murza idanunsa cikin na Akhnan din dake tsaye suna facing juna,har ya kammala saka key din sannan ya riqe qugunta dukka biyun still yana duban wadannan blue eyes din da shima a yau yaga sun qara haske. "Bakiji kunyar cin amanar data bar maka ba?" Ta fada da wani tausashen harshe da lafuzzan nata suka zame masa kamar wata susa a inda yake masa qaiqayi. "That may be my favorite sound.” ya furta muryarsa tana narkewa da salo na rada da wani sauti can qasa da kunnuwanta kawai ya lamuncewa taji,yana maganan idanunsa suna lumshewa tare da budewa gaba daya. "Inda na fada mata zaka iya kare kanka ne?" Ta sake fada idanunta suna sake hada qwalla,tana kallon yadda yake qare mata kallo tsakanin idanunta da lips dinta dake juyawa a hankali. "…what a beautiful sound.” ya sake fada cikin harshen faransanci yana jin yadda muryarta tayi too soft. Maganan da yakeso ta masa.....a yanzun ya sameta,sai yakejin kamar ya riqe lokaci su tabbata a haka ita dashi. "Hais......" Dakatawa tayi ta kasa qarasa fada. Daren jiya.......daren jiya ne ya dawo cikin kanta,daren jiya daya buqaci ta maimaita sunan,kuma tayita maimaitawar cikin rashin sani.....daren jiya da furta sunan ya ajiye mata wani rubutaccen tarihi. Bugu da qari a yammacin yau sai taji sunan ya mata nauyi,sunan ya mata nauyi a harshenta.....sunan ya mata wani daraja da bata taba jinta kusa da ruhinta ba. Ya sani.....ya fahimta sunansa takeson fadi amma ta katse,tun kafin ta qarasa idanunsa suka fara sauyawa. Tun daga jiya yafara qaunar jin sunan daga bakinta. Tun daga jiya yakeji duk duniya a bakinta kawai yakeso yaji sunan. Jawo qugunta ya sakeyi zuwa jikin nasa da wani irin kusanci me barazana ga bugun zuciya dama na qwaqalwa. Tana jin yadda idanunsa suke kanta,tana jin yadda suke musayar numfashi da wani kalar qamshi da hatta a numfashinsa shine cakude a cikinsa. "Say it" Ya sake fada da wannan coolness din,idanunsa suna lumshewa sosai yana kallonta ta qasan idanun nasa. Zuciyarta ta buga,a rayuwa batasan sau nawa zai kasheta ba.....batasan sau nawa yakeso ta mace a kansa ba. Ko har sai tayi hauka?,ko har sai ta fito tana gayawa duk wanda ta sani dama duk wanda ta gamu dashi?. "I....." Ta soma fadi,amma sai ya girgiza kansa a hankali yana qulle idanunsa cikin nata. "Noo" Da wata muryar me zurfi da yake zarcewa tana komawa cikin maqoshinsa. "Say my name" . Ji take kaman zata sume,saita lumshe idonta na daqiqa daya,sannan ta sake budesu slowly. "Haisaamm" Kalmar ta fito da wani irin taushi da amo,sannan ta zarce tana gauraya da shurun cikin dakin. A hankali ya daga yatsansa ya aza saman lips dinta,ya fara zagayasu a hankali,wani irin lallausan qaramin murmushi na gefan baki tana subuce masa. Idanunta ta maida tana sakeyin luuu kamar wadda zata tafi ta suma,saidai ba suman bane.....ita daya tasan irin bala'in da abinda yakeyi yake saukar mata cikin jikinta,ya tayar da kowacce tsiga ta jikinta har tana jin tana tsuma sosai. "Be careful Akhnan......I’m becoming addicted to that voice.” ya fadi yana qarasa hade tazarar dake tsakaninsu ta hanyar manneta a jikinsa. " Ko sau dubu nawa.....ko sau miliyan nawa nake buqatar naji.....don Allah...karkiyi rowar fada" Ya qarasa maganan yana manne fuskarsa jikin dogon wuyanta dake fidda qamshin skin product dinsa. Qamshin da tunda yake amfani dasu sai a yanzun ya soma jin dadinsa.....saman fatarta,lallausar fatar da bai taba zaton akwai jikin wani dan adam da za'a samu da laushi da santsi irin haka ba. Wani numfashi taja sosai tana damqe kafadunsa da duka hannayenta,tana jin kamar yana fusgar wani abu cikin kanta da gangar jikin ta gaba daya. A gefe guda kuma tana jin zazaabin dake jikinsa,zazzabin data dauka ya gayawa nanay ne kawai.....da gaske shine cikin jikinsa. "......my healer.....bani da lafiya" Ya fada yana sake narke mata gaba daya a jiki,kamar duniyarsa batasan komai ba bayan jikin nata. ".....Muje ki bani magunguna na nasha" Ya furta yana daga kansa daga wuyan nata zuwa ga fuskarta ya hade fuskokinsu guri daya. Kalmar MAGUNGUNA daya fadi da kuma zazzabin da taji a jikinsa shine ya cire mata tunanin komai a ranta,cikin rawa murya da neman mafitar samun tazara a tsakaninsu kan yadda ya manne mata da yawa ba tare da tunanin komai ba tace. "Muje". Wani boyayyeb murmushi ya saki ganin bata gane ba,rashin wayonta muraran yana fita,yana jin yana qara raina shekarunta tare da hango kusakurai a ainihin shekarunta. Abinda yafi aminta dashi,ta fara makaranta da wuri,ta kammala da wuri,wannan ya bata iya experience na kasuwanci da iya riqe kamfani kawai........ya dauke hankalinta daga sanin rayuwa da mu'amala. Don ta rayu ita kadai ne ba cikin jama'a ba. Ta rayu cikin kebantacciyar rayuwa ita daya. (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) D'ai d'ai yayi saman gadon yana qare mata kallo sanda take kai kawo kawo tray na maganin da sauran dosage cap din dake ajiye guri daban. Cikin ransa yakejin inama zai iya haqura ya barta ta huta sosai kaman yadda ya tsara......saidai shi kansa yasan a yanxin ba shine yake da control da kansa ba. Zama tayi sosai tana zubawa tana miqa masa. Baiyi musu ba wannan karon ya dinga karba yana shanyewa. Saidai a duk sanda zata d'aga kanta ta kalleshi idanunta cikin nasa suke fadawa. Sanda ta kammala tana daukewa kiran sallah ya ruskesu,sai ya miqe zuwa bathroom ya daura alwala,ya fito idonsa a kanta yana ware hannun rigarsa. "Zaki bani maganin dare?" Ya tambaya idanunsa suna raunana. Still bata kawo komai ba ta gyada kanta a hankali sai ya juya ya fice yana murmushi. Haka kawai ta samu kanta cikin kallon agogo,haka kawai ta samu kanta da liasafa yawan dadewarsa a waje bai shigo ciki ba. Tana cikin lallausan duvet din data lullube har kanta,saboda sanyin Ac dake ratsata daya soma yi mata yawa. Tsoro takeji sosai,zuciyarta kuma a raunane take,don tun bayan sallar isha'i ta soma jin rugugun hadari daya fara hade sararin samaniya. Ba kowa a kusa,batasan inda wayarta take ba ballantana ta kira birra ta kasance a kusa da ita,ko ina akwai.haske tarwai,amma cikin zuciyarta tana jin kamar ita kadai ce ta rage,don haka sai kawai ta shiga toilet tayi wanka taci abinci,sannan ta koma tayi brush ta dawo dakin ji yadda iska ke daga manyan curtains din dake zagaye da dukkan wasu windows da doors na sashen. Cikin sleepwear me kauri ta shirya data zaqulota da qyar a qarshen suitcase dinta. Saidai abun haushin wandon marabarsa da pant kadanne,don duka duka ya tsaye a cinyoyinta. Gwara rigar sakkiya ce me gajeran hannu,round neck ne bata da zip ko button ko daya,wannan shine abinda ya bata nutsuwa da kwanciyar hankali. Bude jakar da nanay ta bata dazu tayi na turaren wutan shuwa incense(+234 704 229 3387),qamshin ya sauka a hancinta da wani irin laushi da taji ya dace da yanayi garin na yanzu. Samun kanta tayi da takawa zuwa ga babbar burner din dake tsaye daidai musallah area na dakin,ta debi turaren wutan ta zuba,abinda bata taba yiba,aiki ne na hadimanta,sunsan yadda takeso guri koda yaushe ya zamana cikin qamshi. Gaban madubin ta koma tana bude khumras din. Kowacce ta shanshana sai taji tayi mata,sai ta dinga budesu daya bayan daya tana zubawa a tafin hannunta ta soma mulke jikinta dasu. Body milk,humra misk,humra sandal,sannan ta hada genani da kulaccam ta sake mulke fatarta dasu. Murmushi kawai takeyi tana jin yadda qamshin ya hadu dana turaren wutar yana gauraye dakin,yana kuma bada wani irin qamshi me saukar da farinciki da nutsuwa a zukata. "Ya salam" Ta fada sanda ta nutse cikin duvet din,dukka qamshin suna ratsata da wani irin yanayi,saidai bata jima ba wani irin kewa da tuninsa suka cika mata zuciya,abinda ya sanyata wannan dubawar da lissafa lokacin,har zuciyarta tayi wani irin shuru kawai yana sauraren yayyafin dake daba glasses din dakunan dake lullube da curtains. Har lullumshewa idanuwansa suke sanda ya fito daga wankan,wankan da yayishi saboda ya samu sassaucin zazzabin da yake d'anji. Wasu sauqaqan silk pyjamas ya sanya marasa nauyi me gajeran wando,saboda gudun saka kaya masu nauyi da zasu sake tunzura zazzabin. A nutse ya tura qofar dakin da wani irin kasala da mutuwar jiki da zazzabi yake saukarwa. Sai ya maida qofar dakin ya rufe a hankali,yanayin da yaga dakin da wani irin dim light yasa ya sanya a ransa tayi bacci. *zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 08187255862 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 08187255862 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽 💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 81* ____________________________ https://chat.whatsapp.com/BkfPzSEDhnsIwyCD8LNGkm?s=cl&p=a&mlu=0 *IDAN KINSAN BA ORDER DIN KAYA ZAKI DINGA SAKAWA BA* *IDAN KINSAN BA BUSINESS KIKE DA NIYYAN YI NA KAWO KAYA DAGA CHINA BA KARKI SHIGA* *_DON ALLAH KARKI BATAWA KANKI LOKACI_* *_Assalamu alaikum my loyal people_* *_Barkanmu da wannan lokaci,kuma barkanmu da warhaka_* *_akwai da dama cikin mata wadanda suke sha'awar yin order kaya daga CHINA zuwa NIGERIA,NIJER,CAMERON,CHAD da GHANA_* *_Amma rashin samun amintaccen company....ko hannun wanda zasu dinga siyan kaya ta hannunsu cikin aminci ya hanasu_* *_To a yau addu'ar da yawa daga cikinku ta amsu,don nayo muku tsarabar kamfanin da zakuyi siyayya ta hannunsu su kuma dora muku kayanku har qasarku cikin aminci ba tare da fargaba ko d'ar d'ar ba_* *_kunsan komai nawa TASTED AND TRUSTED ne,to wannan kamfanin idan akwai abinda yafi TASTED AND TRUSTED ma shine_* *_Baki da fargaba kota sisin kwabo,ni SAFIYYA HUGUMA na tabbatar da hakan_* *_Zaki iya kasancewa dasu group nasu,inda a nan zaki hadu da agent dinsu da CEO nasu gaba daya ta wannan link din,zaki samu bayanansu da komai da ya shafi mu'amala dasu_* *INA ME BAKU TABBACIN AMINCI DA INGANCI DA SAUQIN MU'AMALA DASU DA IZININ ALLAH,BAN TALLATA MUKU SU BA SAI DANA GWADA* *Allah ya dafa mana,yasa mana albarka a nemanmu,ya albarkaci halal dinmu ameen summa amee* __________________________ Yana takowa a hankali idanunsa suka sauka kan magungunansa na dazu,kaman ya biya yasha amma sai wannan kasalar tasa da sakalcin daya saba yiwa nanay ya hanashi,ya yanke gwara kawai ya kwanta a hakan. Remote na Ac din ya dauka ya kasheshi gaba daya,ya matsa ga windows din yana budesu yadda fresh air din zata samu daman shigowa. Bai sani ba.....amma yana ganin kamar batasa muhimmanci fresh air ba,ba abinda yakeso a rayuwarsa sama da fresh air. Yanayin dakin ya gauraya da tatacciyar iskar,sai ya sake maida dakin da wani yanayi na daban me sanyaya zuciya. A hankali cikin nutsuwar nan tasa data dace da kowanne yanayi ya taka zuwa gaban gadon,kai tsaye ya sanya hannunsa ya janye duvet din data rufe har saman kanta dashi. Wannan cute and innocent face din nata ya soma gani,qananun gashin kanta data daure tsakiyar kanta wasu duk sau hauro saman idanunta suna sajewa da wannan zara zaran gashin idanun nata da suka zama tamkar wani fure cikin shukoki a saman fuskartata. Yakai hannunsa a hankali ya shafasu yana janyewa gudun kada ya tadata. "Akhnan" Ya furta can qasan maqoshinsa yana qarewa fuskarta kallo.. Wannan fuskar data riga ta kafe kanta cikin zuciyarsa da wani irin kafewa me matuqar tsaro da qarfi.....wannan fuskar data zama ta farko a duniya gaba daya daya soma yayewa hijabinsa......wannan fuskar data shiga da fita cikin kowanne tunaninsa take hanashi sukuni gaba daya. Fuskar nan dai da a duniya idan ka dauke nanay akwai fuskar data kaita daraja a idanunsa. A hankali ya sunkuya ya bata forehead kiss da tausasan labbansa,sannan ya daidaita mata duvet din ta yadda zata samu numfashi me kyau. Remote ya dauka yana sake rage kaifin dim light din dake fita ta ceiling din dakin,ya maida ya ajiye yana haurawa gadon a nutse. Abubuwa da yawa yakeso.....abubuwa da yawa yake buqata daga gurinta a irin wannan yanayin da yakejin wani baqon qamshi me sanyi a hancinsa cikin dakin. Wani irin qamshi da duk da baida lafiya yaji a hankali yana kwantar masa da hankalinsa da aza masa wata irin nutsuwa. Ya lumshe idanunsa yana jan pillow gefenta yana gwada bada tazara a tsakaninsu yaga idan zai iya. Shuru ya ratsa dakin,shurun daya iya dauko mata sautin fitar numfashinsa da wani irin yanayi daya fusgi hankalinta. Tunda ya shigo dakin ta farka,taji kuma kowanne motsi nasa saidai bata motsa ba,tsoro da fargaba sun hanata. Bata dauka zai sake dawowa dakin ba,tunda sassan cike suke da tarin bedrooms kala kala. Tana jinsa har zuwa sanda ya kwanta da yadda ta soma jin sautin numfashinsa. "Bashi da lafiya tunda ya fita.....kada wani abu ya sameshi" Ta furta can qasan zuciyarta. Wannan dalilin ya sanyata mirginowa kamar me baccin gaske,take kuwa ta samu kyakkyawaan masauki a qirjinsa.....a take kuma dumin daya ratsa fatar fuskarta ya gaya mata zazzabi yake. Irin zazzabinnan dan gaske da kake iya jin hucinsa sosai. A dan razane ta farka ta miqe ta zauna,tanason ta kira sunansa amma bakinta ya mata nauyi,batasan sunan da zata bashi ba,sai kawai ta lalubi remote inda ta ajiye dazun. Bata jishi ba,sai taci gaba da miqa hannunta tana lalube,cikin rashin sani a cikin duhun sai gata dumu dumu cikin jikinsa. "Sanyi nakeji....." Y dakata. "Don Allah" Ya qarasa fada da wani yanayi me karyewa a muryarsa. Adan tsorace take,saita girgiza kanta a hankali. "Haisa...." "Say it please" Ya fada yana qoqarin cusa fuskarsa tsakanin wuyanta. Kafin kuma ta sake cewa komai ya rungumeta a hankali,rungume me cike da buqatar samun nutsuwa. Yaji yadda zuciyarta ke bugawa da sauri,wannan tsoron.....wannan tsoron dai,ya motsa tausasan labbansa ahankali "I need your warmth....." Jin abinda ya fada saita daina mutsu mutsun da takeyi tana qoqarin fahimtar sabon yanayinsa. Zazzabi yake kuma sanyi yakeji yadda tayi a Makkah,yanayi ne mara dadi da kake buqatar dumin wani a kusa dakai kaman yadda yayi.mata wancan karon. Indai bazai rabata da rigarta ba.....zata iya taimaka masa yadda yayi mata a wancan lokacin,saidai a iya yanayin yadda suke kwance a yanzun,fatarta cinyarta me santsi da laushi tana gogar lallausar fatarsa me cike da gargasa,hakan kawai wani abune dake tayar mata da tsigar jikinta. Daure duka wannan abun da takeji tayi,ta daga hannunta ta dorashi a saman bayansa tana bashi comfort sosai. "Finally.....peace" Ya fada cikin zuciyarsa yana jin yadda zuciyarsa ta fara tsatsagewa da yadda a yau tadan tabuka wani abu na jawoshi jikinta da tayi. "Me yasa nake jin kamar wannan shi ne inda nake tsoro… amma kuma nake jin aminci?" Tambayar ta kunce daga cikin kanta sanda wani irin shuru ya ratsa dakin,tana kuma jin saukar numfashinsa a hankali cikin tsakiyar sumarta. Motsawa tayi kadan tana tunanin ko ya samu bacci,amma sai taji ya riqeta da kyau. "Stay please....." Ya dakata. "Just for a moment" Ya qarasa fadi fatar labbansa tana mannewa wuyanta bayan ya sauke kansa kadan. Yarrr taji wani abu ya zuba a jikinta,ta motsa qafarta sai taji ya sanya cinyarsa daya ya raba tsakanin cinyoyinsa yana rungumeta da salon kwanciyar nan ta bear hugs. Wani irin shuru na nutsuwa.....wani irin shuru na qoqarin fahimtar juna,wani irin shuru na kusanci shine ya ratsa tsakaninsu,saidai kuma wannan kusancin yanaso yafi haka zurfi ne.....wannan kusancin yanaso yafi haka nisa,amma bai furta ba,yaci gaba da lafewa cikin jikinta yana zuqe tattausan qamshin shuwa incense and more +234 704 229 3387 wanda ta mulke humras din har cikin gashinta. Kowacce gaba ta jikinta a hankali take amsa rungumar da yayi mata. Shige yanayin daya fara jefata a jiya kafin ya wuce ya bude mata hanyar da batasan yadda ake budeta ba. Tana tsoro kada ya fara koya mata wani daban,gwara tayi nesa kadan dashi ta fara da jinyar zuciyar daya dasa mata wani irin dashe da yake neman fin qarfin control dinta. "Amma magani....." "......zaki bani?" Ya tambayeta yana katse numfashinta. Muryarta na rawa tace. "Eh....shi ya kamata kasha.....ka sakeni na dauko maka" Ta fada cikin qarfin hali tana miqewa. Fincikota yayi a tausashe,sai gata gaba daya ta zube a samansa. Hannuwansa dukka ya sanya ya lullubeta saman jikinta. (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) "Ko kin bani.....wannan maganin bazai aiki ba a nan......basai kinje ko ina ba......I don’t want distance from you… not even in thoughts......maganin yana tare dake". Idanu ta waro waje,tana tuna abinda ya faru jiya "Shi zai maimaita?" Ya gani......yaga tsoron dake cikin idanunta,bayaso kuma yaje mata a haka,sai ya miqe daga kwanciyar still tana cikin jikinsa,ya boyeta sosai cikin faffadan qirjinta.....saidai still ya bata daman daga kanta tana dubansa,don shima haka yakeso.....don shima abinda yake buqata kenan,yaga cikin wadannan qwayar idanuwan dake zautashi kowanne second. "I could lose everything… but not your presence gimbiyata" Ya fada yana narke mata sosai kaman wanda ke shirin fashe mata da kuka. Batasan ya yakeji da tunata kawai ba......batasan ya yakeji ba da tuna irin duniyar data kaishi ba. Yanaso ya barta ta warke a first stage din daya kaita jiya......amma a yanzu a wannan lokacin ya yarda cikakken maqaryaci ne shi da yace zai iya barin nata. Idanunta ta janyw daga cikin nasa,duk da bugun da zuciyarta keyi hakan bai hanata jin tasirin maganar da yake mata da yaren French ba. Ita inda zai taimaketa,daya daina mata magana da French kwata kwata,narkar da ita kawai yakeyi yana kuma sake melting heart dinta,tare da sake dasa mata wani matsanancin sonshi. "Biftuuuu" Ya kirata a lanqwashe yana jan qarshen sunan. "Kinfi komai dana taba samu muhimmanci a rayuwata......I was not looking for love kwata kwata a rayuwata a baya… but you changed the direction of everything" Ya qarasa fada yana riqe fuskarta cikin tafi hannunsa. Ta fara jin tsoro......ta fara jin tsoro da shakkar yadda yake qoqarin karya mata zuciya,yadda yake qoqarin rinjayarta. Ta fara jin fargaba,amma duk da haka ta motsa labbanta. "Mun yiwa nanay laifi jiya da nake ganin kamar ta gano dazu......kuma yansu so kake mu sake maimaitawa?" Ta fadi muryarta na rawa,tana fatan wannan ya zame mata karbabben uzuri. Wani irin murmushi daya qara masa kyau duk da birkicewar da fuskarsa tayi yayi. "Kina zaune kusa da mijinki......amma kina bawa tsoron nanay muhimmanci sama da lafiyata......waya sani ko a wannan lokacin,itama tana kusa da motiii......tana bashi abinda ke kike tsoron bawa mijinki......tana masa abinda ke kike....." Da qarfi ta danna kanta cikin qirjinsa saboda yadda taji kamar yana rikito mata duniya. Kunya mara misali ta rufto mata. Me yasa?,bashi da kunya har haka?,ba zata iya imagining nanay da abinda sukayi jiya da wanda yakeso yayi yau ba. Murmushi ya sake kubce masa,ya fuskanci birkicewarta,sai ya sake riqe fuskarta da kyau. "Ke kikace zaki bani magani.....alqawari kika sakeyi....." "Ina qoqarin yin hakan.....amma bata wannan hanyar ba.....tsoro nakeji.....ina qoqarin koyon yadda zan kula dakai...." Lumshewa kawai idanunsa sukeyi suna budewa akan fuskarta. Bakinta......idanunta da yadda qirjinta ya danne qirjinsa kawai yake iyaji,sai haqurinsa da kawaicinsa daketa sulalewa yana yin nasa gu. "Ki koya a hankali.....amma karki barni lokacin da koke qoqarin koyon...." Ya qarashe fadi da hade bakunansu guri daya yana sarqafe harshenta cikin nasa da wani irin yanayi daya tsaida komai cak daga cikin kanta. Da hucin zazzabinsa.....da rawar sanyin da yakeyi,da kuma yadda yake aike mata zafafan saqonni duka suka cure mata guri daya suka rikitata. Ta rasa a ciki wanne zata banbance?. Tana jin yadda jikinta ke amsar tarin saqonninsa duk da girma da zurfin tsoron dake dawainiya da ita,amma hakan bai hana jikinta amsawa ba. A hankali cikin qwarewa da hikima ya shimfidar da ita cikin sauqi ba tare data shiryawa hakan ba. A hankali kuma cikin hikima ya zare duk wani abu da zai iya zama shamaki tsakanin fatarsa da tata,ya hada da nashi dukka ya cillar,sannan skin na junansu suka maye gurbin wadancan abubuwan. Bata tabbatar da ma'anar kalmar wasa farin girki ba sai a wannan yanayin.....bata tabbatar da ma'anar sharar fage ba sai yanzun daya qarasa maidata cikakkiyar mace wadda taci sadakinta dari bisa dari. Bata gane ba mutuwa zatayi ba saida taji tana numfashi,sannan bata gane ba mutuwar tayi ba saida ta jita cikin ruwa me dumi yana ratsata,wanda bata da wani sauran qarfin da zata iya qwatar kanta musawa ko wani abu daban. Ko sau daya yau bai barta tace komai ba,ko sau daya yau bai barta ta kira sunan kowa. Ya kaita duniyar daya tabbatar ta gama zama tasa.....ya kaita inda dama.bayason ta tuna kowa bare ta kirashi saishi kadai.....saishi muhammad haisam. Tana ji.....tana kuma gani ya juyata yadda yakeso. Tana ji tana gani ya kalli duk inda yakeso,ya taba duk inda yakeso,ya kuma sumbaci duk inda yakeso. Yayi qwallarsa.....yayi murmushi,ya rungumeta iya adadin daya masa,sannan ya shiryata ya gyarata tamkar wanda ya samu 'yar tsanar roba. *zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 08187255862 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 08187255862 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 82* ___________________________ *_Mg's ORGANIC SOAP_* *_Shin kin gaji da banke banken sabulu wa fatarki?_* *_Kullum ba ci gaba?_* *_Kullum jiya iyau sai sake lalacewa ma da takeyi?_* *_matso maza ga maganin matsalanki da izinin Allah_* *MG'S ORGANIC SOAPS* *_kamfanin da ya shirya tsaf don samar miki da sabulun da zai sanya fatarki KYAU ta goge tayi haske ME AJI bana bleaching ko me bata fata ba_* *_KALAN 'YAN ABUJA.....kalar hutu hajjaju,asalin kalar fatarki ta anihin_* *_Masu matsalan SKIN irinsu PIMPLES,SPOT,ACNE,SUNBURN in sha Allah kukanku ya qare....matsalarku ta qare_* *AKWAI PACKAGE DA SUKE HADAWA GAME BUQATA* *yammata.....zaurawa....amare.....da iyayen gida masu capacity wanda ya hada da* Soap Facewash Face cream/body cream Scrub Serum Cleanser Glow oil Toner *duka cikin package din* *_INA MASU FAMA DA NANKARWA(STRETCH MARK)MG'S ORGANIC SOAP bata barku a baya ba_* *Ku nememu kai tsaye a wannan number don GYARA DA MAGANCE MATSALOLIN FATARKU* 0806 299 1549 *MG'S ORGANIC SOAPS* *_takenmu (MAIDA TSOHUWA YARINYA....A SABUNTA YARINYA ZUWA SABUWAR HALITTA)_* _________________________ Sai daya maidata jikinsa ya mata kyakkyawan riqo da zummar su koma bacci,sannan hawaye suka balle mata. Dama.dalilin da yasa ya daukota daga gaban sultane?,ya kawota nan?,ya qirqiri ciwo kuma saboda ya azabtar da ita?. Yayi tunanin ya barta ta rage hawayen saboda zuciyarta tayi sanyi amma sai ya kasa. Ci masa zuciya yakejin ana masa da wani irin yanayi me nauyi. Hannu ya miqa,ya dauki remote ya qara haske kadan na dakin,zuwa sannan ruwan sama ya kece sosai,abu daya daya hana akhnan ce masa yabar mata saman gadon. "Giiftii" Ya kirata da sunan da zuwa yanzu ta fara jin girmansa. Bata amsa ba,dama kuma bai sanya ran amsawar ba,wani yanayi ne daya shirya tunkarar kowanne hukunci ta shirya yi. "I'm so sorry please" Ya furta da muryar da take sirri ce tsakaninsa da ita kawai. Ta bude baki zata kira sunansa da nufin gaya masa ya barta ya qyaleta,amma sai ya girgiza kai. "Ki barni na gama magana...." "Bankai matsayin na zama wanda zai saki kuka ba......ina neman afuwa dana sanya gimbiyar agadez kuka" Ya fada yana kwantar da kansa a hankali saman kanta kamar wanda zuciyarsa ta karye. Ya bawa shuru dama na wasu daqiqu sannan yace. "Na yi kuskure… I should have been more careful.” sai ya dakata. "More gentle.......more patient" Sai ya daga kan nasa ya saka hannunsa yana dagowa da fuskarta. Idanunta a runtse suke alamun batason kallonsa. "Ki sani… ba na jin dadi idan na ga hawaye a idon mace." Muryarsa ta sake wani laushi da zurfi. "Kuma idan har nine dalilinsu....." Sai ya sake dakatawa kamar me zaben kalmomin. "To nafi kowa jin zafi". Wani kyakkyawan sauka kalamansa suke mata saman zuciyarta tamkar saukar fiffike. Taja wata ajiyar zuciya 'yar siririya wadda ta alamtawa haisam zuciyarta ta fara samun nutsuwa da sassauci. "Ki gafarceni....." Shuru "Ba saboda in tilasta miki ba....ko don ke kanki" Ya sauke idanunsa qasan labbanta a hankali. "Because you deserve peace… not confusion.” Tass ta lalubi duk wani fushi daga qasan zuciyarta ta rasa. Kamar yayi amfani da hypo ya wanke farin tufafin da suka baci da datti. "Naji" Ta samu kanta da furtawa a hankali. Murmushi ya saki me taushi,a yau yaga wani other side din nata. Saurin yafiya.....afuwa da zuciya me taushi. "Zonan" Ya fada kaman wata tazara ce me yawa a tsakaninsu yana sake jawota cikin jikinsa. "I'm here now.....just for you....just for your comfort...." Ya sauke numfashi "Kukan ya isa haka.....ki huta" Ya qarasa fada yana sauke mata tattausan kiss dinnan da take jinsa har tsakiyar zuciyarta duk sanda ya sakar mata shi. Wani irin bacci sukayi shi da ita,wani ni'imtaccen bacci daya kusa waftarsa ya kusa wuce lokacin daya kamata ya fita sallah. Wani abune daya manta a rayuwarsa wato ranar daya makara sallar asuba. Dakinsa ya wuce ya sake wanka,don bayajin zai dawo da wuri daga masallaci. Akwai wani issue daya taso da yakeso daga masallacin ya wuce don yayi ya kammala ya dawo da wuri yayi jinyar b'arnarsa. Dan qaramin bincike ne a wajensa da yake ganin awa hudu zuwa biyar sun isheshi ya kammala,dalilin dadewarsa kenan a jiya,ziyarar sirri ne da gwamanan jimma ya kawo masa akan issue. Koda yace awa hudu ko biyar zai kammala,sun yarda dashi,saboda sun san wayeshi. Maye ne kuma qwararre kan aikinsa da wata irin qwarewa ta samu gindin zama a wajensa. Hakanan idan abu zai yuwu zai yuwu,idan baze yuwu ba zai fadi,kai tsaye.....kaifi daya da baya sauya zance. Cikin qatar thobe ya shirya ruwan zuma data color din tayi kama zata saje da launin fatarsa,saidai hakan bai hana bayyanar kyan data masa ba. Har sanda ya dawo dakin yana zuba wannan sassanyan qamshin nasa bacci take. Bayaso ya tadata tun yanzu,kuma bayaso ta rasa sallar asuba,sai ya dauki wayarta ya gyara alarm din da kwanaki ya cire ya qara mata mintunan da zai tasheta yadda lokaci bazai qwace mata ba,lokacin sallar bazai wuce ba. Ya ajiye mata daga saitin kanta kusa da bedside lamp,ya sunkuya softly yayi kissing goshinta yana ja da baya. Wani soyayyarta ce take hudashi da wani irin yanayi dashi kansa baisanshi ba. Wani irin shigarsa take a hankali. A halin yanzu.....a yadda yakejinsa koda quda me cutarwa bayajin zai iya qyaleshi ya sauka a kanta. RAYUWARSA ce muraran yake kalla tsakanin fuskarta,walwalarsa ce.....da DUNIYARSA gaba daya. Yaso ace kafin ya fita ya tattare zanin gadon ya sauya da wani,to amma dole ya barshi,saboda inde zai sauyashi zai tasheta ne abinda baya so,tunda tana da ragowar lokacin da zata iya qara baccinta hankali kwance. Sai daya tsaya ya sake waiwayowa kaman wanda akace masa idan ya fita bazai sake dawowa ya sameta ba,yaja qofar a hankali yana furta. "Fi amanillah" A hankali ta bude idanunta sanda alarm din ke kadawa da tattausan kiran sallar nan daga bakin zaqaqurin ladanin nan,limamin masallacin harami dake makkah. Ba iya siririn hasken da dakin ke dashi kawai ta gani ba,aah......harda lallausan qamshin nan nasa da taji ya cika mata hancinta. Waiwayawa tayi kaman me neman wani abu,ba kowa.....baya kusa da ita,sai pillows da duvet daya barta dashi,sai taji kamar gadon yayi fadi da yawa. Fuskarta ta yamutsa tana jin yadda kanta yayi mata nauyi,dukkanin jikinta babu dadi,yanayi na zazzabi yana son saukar mata,ta miqa hannu ta jawo wayar don katse alarm din,amma saita samu ta hado da wata takarda. Alarm din ta kashe,sannan ta juya takardar tana qarewa rubutun jiki da aka yishi da faransanci kallo. My Healer, _I did not want you to wake up and find silence where reassurance should be._ _Ki yi hakuri da ni._ _Last night is still heavy on my mind._ _Rest today._ _Don’t overthink anything… especially us._ _And my giiftii_ _don’t cry because of me again._ *_Haisam_* Sai wani kyakkyawan Royal sign daga gaban sunansa kadan daya sake janye hankalinta da matuqar burgeta. (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) Duk da tarin gajiya da zazzabin da takejinsa har cikin idanunta amma hakan bai hanata rungume takardar a qirjinta ba tana ajiye numfashi a hankali. Tana jin da dukka kalamansa kamar ya zare komai da takeji. Wannan shine abinda ya bata qwarin gwiwa,ta sauka a hankali cikin takatsantsan ta wuce bandaki. Saidai kafin ta kammala sallar tuni zazzabin da ciwon kai ya dawo ya rufeta,dole ta rarrafa ta koma saman gadon ta rufa ruf har kanta. *_NANAY_* A nutse take takowa zuwa babban parlor din da take sauraren baqi al'umma da sauran mutanen data sahalewa su ganta kowacce safiya. Cikin shigar kamala me daukar hankali gami da nuna zallar dattakonta da haiba kwarjini da kamalarta. Haka kawai tun jiya hankalinta yake kan yarinyar. Duk bayan wasu mintuna sai tunaninta ya fado mata. Cikin girmamawa take sauraren baqin nata gami da sallamarsu,har zuwa sanda kowa ya tafi,ya rage mata ita da zulaihat wadda ta kirata saboda wani kaya da takeso a qarasa qawata sassan akhnan na asalin mansion din haisam da duka kwana hudu suka rage a rakata. Hankalinta ya koma kan obsa,hadimar rumaisa wadda ta qaraso cikin girmamawa. "Ya akayi obsa?" Ta tambayeta hankalinta yana kanta. "Ranki ya dade......yarima haisam ya fita tun safe....suna kyautata zaton sai ita daya......to amma sun yita aike saqo ba amsa daga bangaren nasa da dukka wayoyin dakunan". Idanunta ta qanqantar ciki. "Karfa wani abu yasamu yarinyar nan" Ta fada can qasan ranta,saboda yadda tunaninta yake yawan zuwa mata rai sai takejin kamar ba lafiya ba. "Muje na duba da kaina.....zulahat....ki jirayeni" Ta fada tana miqewa "An gama ranki ya dade" Ta amsa mata sanda nanay ta miqe tana gyara lullubin farin mayafi jikinta. D'aya bayan daya take wuce falukansa tana dosar sassan dakunan baccinsa,abinda ta jima rabonta da tayi,a hankali har qafafunta sukakai qofar dakin. Knocking tayi har sau uku amma taji shuru,sai kawai ta murda handle din tana tura qofar dakin ta sanya qafafunta. Haka kawai yau takejin nauyin shiga dakin a sassan jikinta gaba daya,duk da ta sani baya nan kamar yadda suka mata,amma yau sai take jin kamar wani baqon guri wanda ba muhallinta bane take shiga. Ko ina na dakin fes,yana fidda wannan qamshin nasa. Ta sani dama ko a baya,matsayinsa sam bai sanyashi qazanta ko sakin komai a yadda yaga dama ba. Bama shi kansa ba,har ita yakan kama wasu abubuwan da hadimai ne ya dace suyi amma yayi shi. Saman gado ta hango mutum kwance,kuma ta gane akhnan ce saboda wani sashe na gashinta days bullo ta saman duvet din. Haka kawai take jin akwai wani abu,ta soma nufar gadon a hankali tana dan kiran sunanta,saidai bata motsa ba har zuwa sanda ta isa bakin gadon. A gefe ta zauna,ta saka hannu tana janye duvet din cikin mamakin wacce irin rufa ce haka har saman kai?. Saidai hucin zazzabin daya fito yabi ta iska da hanyar daya samu shine ya bata amsar komai. A dan rikice ta sake kiran sunanta a yanzun dab da ita tana dora hannunta a wuyanta,wannan sanyin hannun nata ya sanya akhnan motsawa a hankali bakinta yana furta. "Hh.....haisammm" Cikin muryar dake dauke da mayen bacci dana zazzabi. Sak nanay ta danyi,sai kuma ta sake kiran sunan nata a tausashe tana hadawa da fadin. "Nanay ce.....momminki" Maganar ya dawo da ita kadan daga duniyar da take ciki. Ta bude blue eyes dinta a hankali wadanda suka sauya kala akan nanay din,saitayi qoqarin daidaita kanta daga baccin wahalar dame fusgarta. "Me yasa zaki kwanta haka ki lulluba gaba daya?,bakyajin irin zazzabin da yake jikinki?,ina shi haisam din ya fita ya barki?" Ta fada tana fada gami da qoqarin cire mata duvet din gaba daya saboda ta samu wadatacciyar iska kada zafin yakai temperature di da ba'aso. "Da yasan ya warware.....me yasa ya kasa maidomin ke kaman yadda mukayi alqaw......." Saita gaza qarasawa saboda sauka da idanunta yayi akan farkn duvet din wanda yabar stain na jini gurare daban daba.....jinin da akhnan din kanta batasan dashi ba ta dawo ta sake kwanciya samansa abunta. *_To kedai nanay ki gani kiyi kamar baki gani ba shine kawai_*🫣🫣🫣 *_Wai yaya labarin sultane ne?,ya yake ciki?_* *_uhmmmm.....akwai kwantacciya a qasa fa.....amma dai....bazan baku satar amsa ba_* *_kuna zaton shurun haisam game da lamarin mammina na lafiya ne?_* *_Fatan alkhairi_* *zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 08187255862 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 08187255862 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 83* _________________________ https://chat.whatsapp.com/BkfPzSEDhnsIwyCD8LNGkm?s=cl&p=a&mlu=0 *IDAN KINSAN BA ORDER DIN KAYA ZAKI DINGA SAKAWA BA* *IDAN KINSAN BA BUSINESS KIKE DA NIYYAN YI NA KAWO KAYA DAGA CHINA BA KARKI SHIGA* *_DON ALLAH KARKI BATAWA KANKI LOKACI_* *_Assalamu alaikum my loyal people_* *_Barkanmu da wannan lokaci,kuma barkanmu da warhaka_* *_akwai da dama cikin mata wadanda suke sha'awar yin order kaya daga CHINA zuwa NIGERIA,NIJER,CAMERON,CHAD da GHANA_* *_Amma rashin samun amintaccen company....ko hannun wanda zasu dinga siyan kaya ta hannunsu cikin aminci ya hanasu_* *_To a yau addu'ar da yawa daga cikinku ta amsu,don nayo muku tsarabar kamfanin da zakuyi siyayya ta hannunsu su kuma dora muku kayanku har qasarku cikin aminci ba tare da fargaba ko d'ar d'ar ba_* *_kunsan komai nawa TASTED AND TRUSTED ne,to wannan kamfanin idan akwai abinda yafi TASTED AND TRUSTED ma shine_* *_Baki da fargaba kota sisin kwabo,ni SAFIYYA HUGUMA na tabbatar da hakan_* *_Zaki iya kasancewa dasu group nasu,inda a nan zaki hadu da agent dinsu da CEO nasu gaba daya ta wannan link din,zaki samu bayanansu da komai da ya shafi mu'amala dasu_* *INA ME BAKU TABBACIN AMINCI DA INGANCI DA SAUQIN MU'AMALA DASU DA IZININ ALLAH,BAN TALLATA MUKU SU BA SAI DANA GWADA* *Allah ya dafa mana,yasa mana albarka a nemanmu,ya albarkaci halal dinmu ameen summa amee* __________________________ Wani iri nauyi taji yana mamayarta,wani irin abu yana taba zuciyarta. "Ya aikata kenan" Abinda ta fadi a zuciyarta jikinta yana wani irin sanyi. Hannu tasa ta maida duvet din tana rufe gurin. Kawai sai taji a yau ita ke kunyar akhnan,ba akhnan kawai ba,hatta da jinin kunyarsa taji tana ji. Shi yasa wannan uban zazzabin ya rufeta?,bai kuma kira kowa ko ya yiwa kowa magana azo a taimaka mata ba?. "Bazaiso ki gani ba....bake ba,kowa ma bazaiso ya gani ba,qilan yanaso ya dawo ya gyara abinsa da kansa ne" Wata zuciyar ta gaya mata saboda sanin haqiqanin halinsa. Ta sani,tabbas inda yasan zata shigo har dakin taga abun bazai taba fita ko nan da can ba. Ta miqe a hankali jikinta yana wani irin sanyi,tausayin akhnan yana saukar mata. Tasan irin yadda yanayin yake da girma da wahala a gurin kowacce d'iya mace......tasan yanayi ne me radadi qwarai. Amma kuma ta wani Fannin wani irin sanyi ne yake ratsata,qauna girma da soyayya mara misali ta akhnan tana ratsata. "Alhamdulillah" Ta fadi can qasan ranta,tabbas safeena tayi haihuwa me kyau.....morsa safiyya tayi halin qwarai da suka iya tsaiwa kan tarbiyyar d'iyarsu har takai budurcinta inda ya kamata a karbeshi. Batasan me ta nanay ta gani ba,saidai kawai taji kalaman bakinta sun yanke,idanunta ta maida ta lumshe,sai kuma taji muryar nanay din a tausashe tana fadin. "Sannu giiftii" Sake bude idanun nata tayi tana dubanta,haka kawai sai taji gabanta ya karye da irin kallon da ta gani cikin idanun nanay din. Kallo ne na jin nauyi hade da tausayi,ba irin kallon data gani dazu bane. "Zaki iya tashi?" Ta tambayeta a tausashe. Da sauri ta daga mata kai gabanta yana faduwa. Ko da ba zata iya ba to tabbas zata tattara dukkan qarfinta ta miqe din don kada nanay din ta gano komai. "To bismillah" Nanay din ta fada tana ja baya kadan ta bata guri. Ta qyaleta ne saboda tanaso ta miqe din taga iya adadin b'arnar da yaro nata yayi. Ta tattakura kuwa cikin gwaninta da jarumta ta tashi daga kwancen,sannan ta fara yunqurin miqewa,saidai tuni ta koma ta zauna tana cije lebe gami da riqe "Wayyo Allah" Da taso fada. "A hankali mana.....karki qarawa kanki ciwo" Nanay data zaburo cikin zafin nama ta fada tana qarasowa gami da riqe akhnan. "Bakiga yadda jikinki yake bane?" Nanay ta sake fadi tana janye duvet din da zai iya hardeta. Tayi qasa da idanunta,tana jin kamar nanay din tana fahimtar komai,saidai kafin takai ga sauke idanunta gaba daya,idanun suka fara haska mata yadda gurare da yawa suka baci jikin farin zanin gadon. Wata irin faduwar gaba ta saukar mata,taji kamar tana daga zaunen jiri zai kayar da ita. "Meye wannan?" Ta fadi cikin sakalci da rashin sanin komai,saidai tana dire tambayar kwanyarta ta dauko mata falaak a wancan ranar. "Innalillahi......na shiga uku" Ta fara maimaitawa a ranta tana curewa guri daya. Itama saida yayi mata irin na falaak din?,tana yabonsa salla ashe alwala ma ya kasa yinta?. Wanne irin babban tashin hankali ne wannan?,Me yasa zai mata haka?,me yasa zai kira mata nanay?,wanne irin tonon silili yayi mata haka?. Ya tsallake hasnaaa ya tsallake rumaisa ya tsallake dukkan hadimai ya kira mata nanay?. Batasan me yasa bayajin nauyin wasu abubuwa ba. Hawaye kawai ya balle mata sabo,ita yanzu da wanne ido zata kalli nanay?,ba zata sake yarda da ita ba.....zataga kaman duka laifinta ne. Don idan bata manta ba ai tace mata ta kula da kanta,ashe abinda take nufi kenan?. Kallo daya kawai tayi mata ta fahimci yanayin data shiga. Ta sani,ko wacece dole a irin wannan yanayin kunya ta dabaibayeta. Ta kasa koda motsa yatsanta,ta wani cure guri daya tana hawaye kamar ta kashe dan mutum. Tausayinta da qaunarta suna sake narkar da zuciyarta,sai kuma murmushi ya subucewa nanay din mara sauti. Murmushin alfahari da ita.....murmushin nasarar samun suruka irinta. Ba shakka kunya wani abu ne.....kunya adon diya mace ne.....kunya tana burgeta idan ta ganta tattare da d'iya mace. Hannu tasa ta cire cliff din da aka riqe zanin gadon dashi na gefe guda,ta sanya hannun ta tattareshi can bata iya inda akhnan din bata zaune a kai. A tausashe ta kamo hannunta ta riqe cikin nata,abinda ya sake yawaita kukan akhnan din harda dan sauti. Shuru ya ratsa tsakani,har yanzu dariya akhnan din ke bata,murmushi take me gauraye da tausayinta. "Ai kukan ya isa haka ummm takwara?" Ta furta a tausashe. "Karki kuka da yawa,kanki zaiyi ciwo......kiyi haquri a madadina a madadin muhammad haisam.....muna nema masa afuwa" Wannan maganar data fada ta qarasa sanya akhnan ta narke gaba daya,wani sabon kukan ya sake zuwar mata. Shikenan.....ya fadawa nanay din ma,bashi da kunya ta rantse baida kunya,a yanzu ta sake yarda da haka ta kuma sake tabbatarwa. A nutse nanay ta janyota cikin jikinta ta rungumeta sosai,kuma bata sake cewa komai da ita ba ta barta sai dataji sautin kukan ya sassauta sannan ta fara magana cike da dattako da nutsuwa,har a sannan tana rungume da ita. (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) "Wajibi ne akan dukkan macen data kawo mutuncinta gidan mijinta ta fuskanci irin wannan wahalar daga farko.....duk da tana wucewa ne a hankali kamar bai taba faruwa ba......akwai wahala,amma alfarmarki kenan......alfarmar diya mace kenan da bata da kamarshi har abada. Alfarmar da ba wadda zata sameta......martabar da babu wadda zata sameta sai wadda ta kaiwa mijinta halalinta wannan budurcin. Wani alfahari guda daya da koda bayan shekara dubu ne zaki iya kallon qwayar idanun mijinki ki goranta masa.......kiyi wannan alfaharin ki sake maimaitawa. Koda ya musa komai daga gareki,koda ya musa dukkan alfarma a nan bashi da abun cewa. Ki godewa Allah daya sanyaki cikin matan da suka rabauta da wannan DARAJAR da ALFARMAR......" Sai tayi shuru tana sauke numfashi. "Alhamdulillah" Ta samu kanta da fada can qasan zuciyarta. Wani irin kwantar mata da hankali maganganun nanay sukayi,wannan shine yake bata tabbacin abinda ya fada a jiya. Kowanne miji da mata da gaske sunayi kamar yadda yace da ita a jiya. Kenan kowa boyewa yakeyi yana shuru?,kuma haka kowacce takeshan wannan wahalar amma taga sunci gaba da zama shekara da shekaru da mazan?. Kamar nanay din tasan abinda take tambaya a kai tace. "Wannan wahalar.... Wannan tsananin na dan lokacine,kada ki damu,zaki daina jin komai.....kinsan me nakeso dake?" Ta fada tana dago akhnan din daga jikinta tana duban fuskarta. Kanta ta girgiza a hankali ba tare data iya yarda ta kalli idanun nanay ba. "Ki dauka a ranki safeena da safiyya ne dukka a nan" Ta furta tana nuna qirjinta. "Duk da ban rayu dake ba,amma nima kamar uwa nake a wajenki.....da wannan idon nakeso ki kalleni,da wannan zuciyar nakeso ki saki jiki dani. Zan miki abinda zanwa su rumaisa da Aanani,don baki da maraba dasu a gurina. Ni ba surukarki bace daga yau.....ni mahaifiyarki ce......uwa nake a gareki" Kanta ta gyada a hankali,tana jin wani irin nutsuwa da gamsuwa suna mamayarta. Wayarta taga ta dauka,tayi kira hadi da yin waya na duka duka mintinan da basufi biyu ba sannan ta ajiye. Riqeta tayi ta sauka daga kan gadon,ta maidata saman sofa ta zaunar da ita a hankali tana bibiyar yadda taka taku a hankali,abinda ya sake ninka tausayinta cikin ranta kenan. Tana zaune daga saman sofa din kanta a qasa tana kallon yadda ta tattara zanin gadon da kanta,ta bincika ta samo wani cover me zip me kama dana bedsheets din ta turashi a ciki tayi zipping nasa sannan ta dauko wani sabo. Batakai ga shimfidawa akayi ba akayi knocking qofar. Kai tsaye ta bada damar shigowa. Dattijuwar macace sosai,wadda tana dan yawan ganinta a sassan nanay sosai. A shekaru zata bawa nanay din shekara kusan biyar,saidai duk da yanayin tsufanta jikinta ya nuna qaqqarfa ce,irin tsufan nan me kyau da yake nuna lallai mutum yana gyara kanshi da jikinsa. "Qaraso mama" Nanay ta fadi tana buda mata qofar,ta shigo da sallama. Koda nanay bata gaya mata ba tasan akwai aminci da kusanci sosai tsakaninsu da matar. Daga gidan sarauta ta fito,ta san duk wanda zaa budewa qololuwar daki irin haka ya shigo tabbas amincin yakai qarshe. Wata leda ta karba daga hannun mamar wadda take ta yiwa akhnan sannu lokaci lokaci,sannun data sanya take sake jin nauyi kamar ta narke a gurin. Nanay bathroom din ta koma,ita kuma maman ta soma gyara gadon,nan da nan ya koma yadda yake. Daidai sanda nanay ta fito,ta dauki jakar zanin gadon ta bawa maman suna magana da yaren oromo,sai.maman ta juya ta fita. Ita ta riqe akhnan,ta shiga da ita bathroom din. Cikin bathtub din dake cike da wani ruwa me wani irin launin kala ta taimaka mata ta shiga,sai tayi tsaye daga gefe sanda akhnan din ke nutsewa cikin ruwan idanunta a rufe. Duk daya gasata sosai dazu,amma a yanzu sai taji ruwan yana shiga jikinta da wani irin yanayi,wadannan cinyoyin nata da takejin qashi ne kawai ya riqesu dumin ruwan dana abinda ke cikin ruwan yana ratsasu har wani lumshe idanu take. Sau uku ana canza ruwan da wasu kalolin abubuwa,sannan daga qarshe ta tara mata ruwa me dumi sosai. "Ki sakeyin wanka don kiji qwarin jikinki sosai,ina jiranki" Ta fadi tana ja mata qofar bayan ta fice daga bandakin. Koda ta miqe tana wanke jikinta sai taji jikinta gaba daya ya saki,ciwon da takeji *zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 08187255862 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 08187255862 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 84* ______________________________ https://chat.whatsapp.com/BkfPzSEDhnsIwyCD8LNGkm?s=cl&p=a&mlu=0 *IDAN KINSAN BA ORDER DIN KAYA ZAKI DINGA SAKAWA BA* *IDAN KINSAN BA BUSINESS KIKE DA NIYYAN YI NA KAWO KAYA DAGA CHINA BA KARKI SHIGA* *_DON ALLAH KARKI BATAWA KANKI LOKACI_* *_Assalamu alaikum my loyal people_* *_Barkanmu da wannan lokaci,kuma barkanmu da warhaka_* *_akwai da dama cikin mata wadanda suke sha'awar yin order kaya daga CHINA zuwa NIGERIA,NIJER,CAMERON,CHAD da GHANA_* *_Amma rashin samun amintaccen company....ko hannun wanda zasu dinga siyan kaya ta hannunsu cikin aminci ya hanasu_* *_To a yau addu'ar da yawa daga cikinku ta amsu,don nayo muku tsarabar kamfanin da zakuyi siyayya ta hannunsu su kuma dora muku kayanku har qasarku cikin aminci ba tare da fargaba ko d'ar d'ar ba_* *_kunsan komai nawa TASTED AND TRUSTED ne,to wannan kamfanin idan akwai abinda yafi TASTED AND TRUSTED ma shine_* *_Baki da fargaba kota sisin kwabo,ni SAFIYYA HUGUMA na tabbatar da hakan_* *_Zaki iya kasancewa dasu group nasu,inda a nan zaki hadu da agent dinsu da CEO nasu gaba daya ta wannan link din,zaki samu bayanansu da komai da ya shafi mu'amala dasu_* *INA ME BAKU TABBACIN AMINCI DA INGANCI DA SAUQIN MU'AMALA DASU DA IZININ ALLAH,BAN TALLATA MUKU SU BA SAI DANA GWADA* *Allah ya dafa mana,yasa mana albarka a nemanmu,ya albarkaci halal dinmu ameen summa amee* _________________________ Sanda ta kammala saita kasa fita,ta nade jikinta da towel kawai tana tsaye tana duban madubi. Ji take kamar ba zata iya kallon idanun nanay ba,duk da qwarin gwiwar data bata,amma kunyarta takeji kaman tayi yaya. Sau biyu nanay na mata knocking. "Da matsala ne?,ko na shigo?" Sannan ta murda handle din ta fito kanta a qasa. Tsaf nanay ta taimaka mata ta shirya cikin wata riga me matuqar daukan hankali. Daga yadda nanay ta fiddata daga wani akwati na musamman ta tabbatar ta musamman ce. Gaban madubi nanay ta jata,ta kuma zaunar da ita gaban madubin bayan ta ja mata kujera ta zauna. Tsaiwa tayi daga bayanta tana duban fuskarta. "Wannan rigar.....motii ya mallakamin ita ne a ranar dana kai nawa mutuncin gidansa kamar yadda kika kawo naki. Na kuma yi alqawarin zan damqata ne kyauta halak malak ga matar d'ana na farko wadda tayi kwatankwacin abinda nayi,saidai shidin Allah baiyi me dogon kwana bane.....na sake ci gaba da ajiyarta da wannan burin,ashe zata zama.mallakin diyata ce. Allah yayi miki albarka,ya baku zuriyya dayyiba.....Allah ya jiqan safeena ya kyauta makwancinta. Allah ya hademin kanku.......ya baku dawwamammen zaman lafiya" Takai qarshe tana buda tafin hannun akhnan din ta saka wani abu da akhnan din bata fahimci meye ba. "Kome zan baki bazan biya farashin kyautar da kika yiwa d'a na ba......na gode....na gode" Sunkuyar da kanta tayi tana jin kamar zata nutse a gurin,sai nanay din ta sanya hannunta dukka biyun ta dagata. "Zan wuce dake sashena,don ki samu ki huta sosai" Har qasan ranta taji dadin hakan da nanay tace,amma sai kuma takejin wani iri sanda suke takawa cikin nutsuwa da rakiyar hadimai suke barin sashen haisam din zuwa sassan nanay. Wani kebantaccen bangare aka bata cikin sassan nanay,don dakin da parlor din qwaya biyu ne tak amma sunfi qarfin a kirasu daki ciki da parlor kawai. Dab yake da dakunan nanay,saidai akwai lubby daya rabasu kadan,nata yana daga hannun hagu,na nanay yana daga hannun dama. Ta lura tun kafin su qarasa hadimai da yawa suka kammala gyaran gurin tsaf,nanay da kanta ta shigar da ita,sai a sannan birra da zenebe suka qaraso. "Ki kula da ita.....ku barta ta huta sosai" Umarni na qarshe da nanay ta bayar kenan. Hakan kuwa sukayi,sun samar mata da wani yanayi me dadi daya sanyata kwanciya bacci cikin nutsuwa,bayan nanay tasa an kawo mata wani irin farfesun naman da batasan ne meye ba,da wani abu sha me yaji yaji kadan da yafi mata kama da tsumi ko mad'i. Sai wani babban abun rufa me wani irin dumi daya dade a jikinta,wada tana cireshi taji kowacce gajiya ta jikinta tana sauka,sannan zazzabin jikinta yana yin nasa guri,ba jimawa kuwa wani irin bacci me dadi yayi awon gaba da ita. *_HAISAM_* A yau ya kalli agogon dake daure a tsintsiyar hannunsa har baisan adadin sau nawa ba. Aikin da yake ganin zai kammalashi cikin awa uku ko hudu,sai gashi yana dosar awa biyu ba tare dayakai inda ya kamata ace yakai cikin awannin ba. Yana cika awa biyu dole ya dauki hutu,ya wuce resting room da yake manne da katafaren office dinsa dake cikin hukumarsu dake addis ababa.. A nutse ya zauna saman tausassar sofa din dake dakin,ya zare socks dinsa yana daukan wayarsa wadda duka hankalinsa yana kai. Duk bayan mintuna sai wannan cute face din nata ya dawo masa,yadda take jage jage da hawaye. Ya lumshe idanunsa yana budewa. Daren jiya ne ke dawo masa fes cikin kansa. Moments din gaba daya,wani irin yanayi daya gaza barin kansa,ya kuma rushe tarihin kowanne dare daya taba kashewa a tare da ita. Banda babban dalili baiga abinda zai sanyashi biyo jirgi tun sassafe,ya baro gefanta ya taho addis ababa da safiyar daya kamata ace tana kwance cikin jikinsa tana hutawa ba. Kiranta yakeso yayi direct,amma yana tunanin kada yaje bacci takeyi ya tasheta,don haka ya zauna a nutse ya rubuta saqo yana tura mata. _"I hope the tears are gone now._ _I did not like leaving you that way this morning."_ (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) Wayar ya ajiye a gefa bayan ya cireta daga silent. Yana sanya ran jin amsa ko yaya daga gareta,ya miqe yana isa dan dining area din dake cikin setting room din riqe da wayar a hannunsa. Black tea ya samu kamar ko yaushe,kamar yadda me kula da cimarsu yake tsananin kula da tsrin cin abincinsa da yanayin da yafiso. Black tea ne da aka noma ganyan da komai ma daga yankin oromo,wani abu da baya nisa dashi,shi yasa yasha wahala sosai a agadez kafin ya saba da kalan nasu shayin,inda daga qarshe dole yasa aka shigo masa da nasu ganyen a boye. Abun mamaki a yau sam baya gane test din shayin,duk da yasan irin qwarewar cook din wajen iya sarrafa shayin. Daren jiya kaf ya dauke taste din a harshensa,tunaninta da gilmawar fuskarta cikin idanunsa gaba daya ya dauke nutsuwarsa. Yana dire mug din ya sake jawo wayar kusa dashi,daidai sanda kira ya shigo wayar tasa da wata baquwar number. Kaman bazai daga ba,amma sai ya tuna koma waye ya iya samunsa yana da alaqa sosai dashi. Don haka ya danna koren alama sannan ya sakata a hands free,yayi relaxing sosai cikin kujerar da wannan nutsuwar tasa yana jin wata kasala tana saukar masa daga tuna iya daren jiya kawai. Muryar macace,mamaki yadan nuna kadan saman fuskarsa sanda take gaidashi. "Abbi ya gayamin ka shigo addis ababa ko?" Tambayar tadan daure masa kai,ya motsa labbansa a hankali. "Wacece?" Yayi tambayar kai tsaye. Shuru ta danyi na wasu sakanni,kaman alamunta suna nuna tambayar batayi mata dadi ba. "Menelik ce" Ta fada a sanyaye. Sunan ya maimaita sau daya sau biyu a kansa kafin mamallakiya sunan ta harba cikin kansa. "Ayyah...." Ya fada a nutse yana jin tun bata sake cewa komai ba muryar ta ta gundureshi. "Ya familynki" "Alhamdulillah.....abbi yace na maka magana ko zakaci abincin dare tare damu?". Zamansa ya gyara a hankali,yana jin yadda zuciyarsa ke sake azalzalarsa da son jin muryar akhnan. " I'm sorry.....ba dadewa zanyi ba.....banajin zan sake awa uku a addis ababa,na gode qwarai,ki gaida abbi din,idan na sake shigowa zamiyi magana dashi" Ya fadi a kalmominsa a jajjere nutsuwar dake sake zurfafa soyayyarsa a zuciyar menelik din. "Nima na gode....." Ta fadi duk da zuciyarta ta quntata da kalar amsar daya bata. Ba haka taso taji daga bakinsa ba,yadda ta iya jurewa rashin ganinsa na wadannan watannin bata dauka zai tankwabe cin abinci dare tare dasu ba idan tayi masa tayi. Ta sauke ajiyar zuciya da alama tafiya ce miqaqqiya a gabanta. Ko digon nasara guda daya bata hanga tattare dashi ba.......amma a yanzun tana jin ta shirya bayyana masa kanta kawai a wuce gurin. Shi ya yanke kiran ba tare daya tsaya ya qarasa jin kalmominta na qarshe ba. Ya sake duba bangaren massages,ba wani sabon saqo daga gareta,kawai sai ya yanke ya kirata yana kashingida sosai ciki sofa din. Tun a kiran farko computer ta gaya masa wayar a kashe take. Yana daga kashingide amma sai ya miqe sosai ya zauna yana sake maimaita kiran,kamar bai yarda da abinda na'urar take gaya masa ba. Karon farko a rayuwarsa daya maimaita kiran wata number kusan sau biyar duka lokaci daya. Kawai sai ya miqe a hankali yana takawa sannan yana laluben wayar hussam. Tuna yanayin daya barta yayi,wani zargi ne ya d'arsu a ransa,ya lumshe ido yana fatan ba haka bane sanda wayar hussam ta fara ringing. Kira biyu ya masa amma bai dauka ba,a sannan yanajin kamar yaje ya jawo hussam ya lakada masa duka haka yakeji. Maida akalar kiran nasa yayi ga abdii,kira biyu tal ya dauka yana gaidashi. A nutse ya amsa Kamar a cikin nutsuwar tasa yake. "Ka dubamin giiftii ta sassan nanay mana". "Tana sassan nanay tare da ita" Ya bashi amsa a taqaice yana gajarta masa wahalar da yaketa yi da tunaninsa. "Ya salam" Ya fada cikin ransa,yaushe ta fita zuwa sassan nanay?,ya tambayi kansa. Yana gujewa wani abu,ya sani nanay tana da doka da qa'ida na son cika al'adu,baiso haka ba,yaso tayi zamanta ta jirashi ya dawo koda zataga nanay. Yayi imanin indai nanay ta fahimci wani abu cikin daya biyu. Kota qara kwanakin bashi ita.....ko kuma ta dauketa har sai ta cika wadannan kwanakin,shi kuma abinda bazai iya jurewa ba kenan. A yanzun bayajin akwai wani yanayi duk girmansa da zai iya jurewa ya raba tsakaninsa da ita. Bazai iya ba ya sani,bazaiwa kansa qarya bama. Ko a yanzun yanajin kamar ya sanya nisan tazara me tarin yawa ne a tsakaninsu. "Hello obbo" Abdii ya fadi jin shurun yayi yawa. "Tu yaushe abdii?". "Kusan awa uku" Amsar abdii ta gama haska masa komai. Idan ta fita ne don gaida nanay zuwa yanzu ya kamata ta koma. Sai a sannan ya tuna,yau din sukayi da nanay zai maidata,tazo ta dauketa kenan. "Shikenan.....zan sake kiranka idan akwai buqatar hakan." "To a dawo lafiya" Abdii din ya fada. Komawa yayi da baya ya sake zama,ya kamata ya zama cikin shiri kawai. Nanay tayi nata shirin shima yayi nasa,da ranshi da lafiyarsa dai bazai bari nanay ya dauke masa mata har sai bayan wasu kwanaki ba. Wayar ya sake budewa,ya shiga contact,yatsansa ya tsaya daidai kan wata number dake dauke da sunan abbool. Bugu biyu ya dauka cikin girmamawa yayi masa sallama. Da sassanyar muryar nan tasa ya amsa masa. "Ina hussam ya shiga?" Ya tambayeshi kai tsaye. *zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 08187255862 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 08187255862 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 85* __________________________ https://chat.whatsapp.com/BkfPzSEDhnsIwyCD8LNGkm?s=cl&p=a&mlu=0 *IDAN KINSAN BA ORDER DIN KAYA ZAKI DINGA SAKAWA BA* *IDAN KINSAN BA BUSINESS KIKE DA NIYYAN YI NA KAWO KAYA DAGA CHINA BA KARKI SHIGA* *_DON ALLAH KARKI BATAWA KANKI LOKACI_* *_Assalamu alaikum my loyal people_* *_Barkanmu da wannan lokaci,kuma barkanmu da warhaka_* *_akwai da dama cikin mata wadanda suke sha'awar yin order kaya daga CHINA zuwa NIGERIA,NIJER,CAMERON,CHAD da GHANA_* *_Amma rashin samun amintaccen company....ko hannun wanda zasu dinga siyan kaya ta hannunsu cikin aminci ya hanasu_* *_To a yau addu'ar da yawa daga cikinku ta amsu,don nayo muku tsarabar kamfanin da zakuyi siyayya ta hannunsu su kuma dora muku kayanku har qasarku cikin aminci ba tare da fargaba ko d'ar d'ar ba_* *_kunsan komai nawa TASTED AND TRUSTED ne,to wannan kamfanin idan akwai abinda yafi TASTED AND TRUSTED ma shine_* *_Baki da fargaba kota sisin kwabo,ni SAFIYYA HUGUMA na tabbatar da hakan_* *_Zaki iya kasancewa dasu group nasu,inda a nan zaki hadu da agent dinsu da CEO nasu gaba daya ta wannan link din,zaki samu bayanansu da komai da ya shafi mu'amala dasu_* *INA ME BAKU TABBACIN AMINCI DA INGANCI DA SAUQIN MU'AMALA DASU DA IZININ ALLAH,BAN TALLATA MUKU SU BA SAI DANA GWADA* *Allah ya dafa mana,yasa mana albarka a nemanmu,ya albarkaci halal dinmu ameen summa amee* _________________________ "Yabar wayarsa ya tafi raka wasu baqi da suka kawo sample na turare sukeso kamfani ya fitar musu" Kansa ya gyada a hankali,yasan da zuwan baqin,kuma shine yace su samu hussam su gama maganar. "Kace masa ya duba wayarsa yanzun.......inaso a dubamin available ticket zuwa dubai tsakanin kwanakin ukunnan,ka gayamin na yaushe da yaushe aka samu saina fada maka wanda zaka yankamin".. "An gama obbo" Ya fada da tarin girmamawar da ita kadai ta isa ta gaya maka adadin girman da yake dashi. Kwata kwata sai yaji zaman addis ababa din ya gundureshi,bayajin koda ya zauna zai iya ayin aikin yadda ya dace,don haka ya soma takawa qafarsa babu ko takalmi yana komawa office din nasa ta qofar dake maqale da resting room din. Yaja kujera saidai bai zauna ba,ya qara laluben wata number ya kira. Shima dai bugu biyun ya dauka da sallama. "Ka dubamin wanne private jet ne available kayimin booking zuwa jimma.....if possible kada ya haura awa daya" "Yanzu in sha Allah" Ya amsa masa,sai ya kife wayar yaja kujerar zuwa gaban system din gabansa ya fara tattara bayanan daya fara aiki a kansu yana maidasu documents. Ya shiryasu don ya turawa bobbo muhammad dawud ne. Sai yanzun ya gane ma'anar hutun da ake bawa angwaye. Shi baima sani ba sam,ya dauka a ranshi hutun na lalaci ne kawai,sai yanzu ya fahimci muhimmancinsa. Ya karbi hutunsa yanzu kam hannu bibbiyu,zai cinyeshi harda qari ma,saboda yanaso ko sanda zai dawo sosai cikin office dinsa ya kammala da duk wani issue daya shafi agadez. Yana cikin aika bayanan wayar tasa ta sake qara,ya daga ya barta a hand free. "An samu jirgin,amma sai nan da awa biyu zai tashi" Ya fada a ladabce. A hankali ya lumshe idanunsa,yana liasafa awa biyun nan cikin kansa. Jinta yake kaman adadin tsahon shekara biyu. A yanzu a yadda yakejin kansa.....inda yana da iko ya kulle idanunsa kawai ya ganshi a gabanta. "Alright" Kawai ya amsa masa a taqaice,kuma wannan amsar ta isarwa abbool cewa a shirya jirgin kenan. Iska me zafi ya furzar daga bakinsa sanda ya kammala aike duka documents din,sannan ya rubuta gajeriyar wasiqa ya aikewa bobbo muhammad dawud ta e-mail dinsa,ya kashe dukkan wata na'ura ya daura alwalar sallar la'asar ya fita zuwa masallacin cikin hukumar. Yadan kashe wasu mintuna talatin a masallacin wai don ya rage lokaci kafin ya dawo office din. Bayason hayaniya wani lokaci ko dogon magana,yau kuma akwai qananun ma'aikata da yawa cikin hukumar da suka sanya masallacin ya zama noisy. Daidai da office dinsa yana da wani irin tsarin gini ne da idan ka shiga ciki ba zakasan abinda ke faruwa koda a bangon office din nasa ba na hayaniyar mutane. Ya tsaya qofar ta kammala scanning nasa zai wuce,daya daga cikin messengers dinsa ya qaraso dauke da wani kwando. "Ranka ya dade......saqo ne aka kawo,yanzun nan dan saqo ya juya ya tafi ganin baka dawo ba" Yayi maganan yana matso da basket din gaban haisam. Idanu ya zubawa basket din sosai,sannan ya maida dubansa ga messenger din. "Waye ya kawo?". " Ban sanshi ba ranka ya dade.....amma dai yace idan aka baka katinnan zaka gane waye" Ya nuna dan card din dake ajiye saman kwandon. Sunkuyawa yayi ya dauki katin a nutse yana budewa. Cikakken sunanta dana mahaifinta daya gani ya fahimtar dashi daga inda saqon yake. Da yace bazai samu daban kaiwa sama da awa uku ba,bazai zauna cin abincin ba shine aka biyoshi dashi har nan?. Katin ya maida saman kwandon ya ajiyeshi kaman yadda yake da farko. "Joseph" Ya kirashi da nutsatsiyar muryarsa me zurfi data sanya mr Joseph shiga hankalinsa. "Na'am yallabai" "Ka manta dokokina?" Ya tambayeshi a gajarce. "Ban manta ba ayimin afuwa ranka ya dade" "Baka manta ba.....amma ka karya.....me yasa?" Ya tuhumeshi hadi da bashi daman kare kansa duka lokaci daya kamar yadda dabi'arsa take. "Bayanin da yayi da cewa kasan wanda ya aiko da saqonne yasa na karba,amma ayimin afuwa,in sha Allah bazan sake bari wani abu makamancin wannan ya sake faruwa ba" Baice komai dashi ba ya fara wucewa ciki,yanaso ya tambayeshi ya za'ayi da abincin amma kwarjininsa ya hanashi,sai dab da zai rufe qofar ya jishi yana fadin. "Ka daukesu daga nan,duk yadda zakuyi kuje kuyi dashi" Ya maida qofarsa ya kulle. Saman table dinsa ya koma ya zauna da tunanin ko zai duba wani abun ya sake ragewa amma sai ya kasa komai. Tsakanin bakin glass view na office din dake haska masa harabar hukumar sosai,zuwa zama saman table sofa da shan coffee baisan wanne yafi yi da yawan adadi ba,baisan ya shanye shayinsa duka ba sai da yaje zai qara ya danna coffee maker din yaji shuru maqatau. A hankali ya shafa sumar kanshi yana sakin wani wahalallen murmushi. Shi kansa mamakin kansa yake. Abun kamar asiri?,ya zama wani very depressed haka?,duka duka har yanzu baikai awa shida da rabuwa da ita ba. Can qasan ransa ya lalubi abinda yafi daga masa hankali NANAY ce. Ya sani kunya ba zata bar ta ta iya fita kai tsaye har gurin nanay ba,hakan yana nufin da kanta nanay taje ta sameta kenan. Taga wannan yamutsatsen gadon?,taka d'iyarta duka a yamutse?. "Ya salammm" Ya fada yana jin nauyin nanay din tun kafin ya hada idanu da ita. Saidai yana ji a ransa muddin ta dauke masa mata ne,hakanan zai runtse idanunsa ya tunkareta ya kuma dauke matarsa,koda ta wata hanyar daban ce. Agogo ya sake kalla,awa daya ya rage masa,yaja siririn tsaki,lokacinma kamar baya gudu,sai ya bulla dressing room dinsa kawai ya soma sauya kayansa zuwa trouser da wata tattausar long sleeve shirt. Sumarsa ya sake gyarawa sosai,ya canza takalmi da agogo duka. Cikin qasa da minti hudu saiga giant sheikh dinnan ya sauya kamar hawainiya. Sau tari mutane sukan rasa banbamcewa tsakanin manyan kaya da qananu wanne yafi masa kyau,duk da yawan shigarsa ta manyan kaya ce,musamman idan yana jimma. Amma idan yazo addis ababa yana sauyawa da duk kalar shigar da yakeso. Already drivensa yana jiransa. Ya bude masa murfin motar yana masa barka da fitowa. Hankali kwance ya shiga,don ba wanda ya bari yasan ya fito da yanzun suna biye dashi kafin su barshi ya fita haka salin alin saiya sake bata wasu lokutan,shi yasa kawai ya fita ta qofar baya. "Gida zamu wuce?" Ya tambaya da girmamawa. "Airport" Ya amsa masa a taqaice yana duban hanyoyin da wani screen a motar ya nuna masa ba cunkoso da adadin tsaron da yake kai da adadin mintunan da zasu cimma airport din. *J I M M A* K'arfe takwas na dare da mintuna ashirin motar masarautar ta shigo dashi katafaren harabar masarautar aba jifar din dake dauke da haske tarwai......da tarin security da wani irin tsaro da yasha banban da kowacce masarauta dake kusa da yankinsu. (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) A daidai lokacin da ita kuma take tare da nanay. Can cikin bedroom din nanay din da wannan shine karon farko data taba tako qafafunta. Wani irin tsarin dakin bacci da qiris ya kusa maidata 'yar qauye......ya maidata tunaninta baya tamkar ba daga masarautar agadez ta fito ba. Cikin wasu lausasan kayan bacci take,farare qal masu wani irin gashi gashi me tsananin laushi dukka jikinsu. Da farko ta dauka zasuyi nauyi ko zasu dameta,amma data sanyasu sai takejin kamar bata taba saka wasu kayan bacci data matuqar jin dadinsu irin haka ba. Hira suke wata irin hira da take sake sakawa akhnan nutsuwa da nanay. Tarin qaunar matar da kimarta da martabarta dukka cikin idanunta. Labari take bata akan mamminta.....mammi safeena. Komai da take gaya mata a yanzu sai takejin kamar sanda yake faruwa tana gurinne. Quruciyarsu......rayuwarsu da yadda suka taso,saidai jikinta kuma ya fara sanyi da yadda nanay ta gangaro kan nau'ikan qalubalen da mamminta ta taba fuskanta a rayuwarta. Aurenta da ajani.....gallazawar kishiyar da sunanta yayi tsaye cak cikin zuciyar akhnan. ZEENATU take wata qaqqarfar tsanar sunan kanta ya shigeta. Dan uwanta dako suna bashi dashi da aka rasa cikin asibiti......barazana daga wancan matar me suna zeenatu din,take taji hadin fruit din da nanay din ta bata tace tasha ya fita duka a kanta. Murmushi kadan nanay tayi tana goge qwallarta. "Komai ya riga daya wuce kada ya dameki,kuma ni da duk wanda ya rayu da ita muna kyautata mata rahamar Allah. Macace me wani irin nagarta......kiyi qoqari kawai kiyi koyi da nagartarta". Kawai sai taji tana kunyar kanta da kanta. Dukka wadannan abubuwan mahaifiyarta ta fuskanta?,harda auren mutumin da bata shiryawa ba?daga mahaifin da baisan wata wahalarta da girmanta ba,auren mai mata har biyu itace ta uku?,ta karba bata musa ba......amma ita fa?. Ta nemi bijirewa sultane.....sultane din daya sadaukar da komai saboda farincikinta. Sultane din da komai zaiyi yana duba maslaharta,ta hambarar da dukka zabukansa.....sannan ta tattare qafar wandonta dana hannu zata tankwabar da zabinsa na qarshe.....zabin da a yanzu zuciyarta a kowacce rana take gaya mata BAKI GAMA SANIN WAYE BA. Zabin da ko a yanzun komai ya qare.....komai ya datse tayi imanin da gaske sultane masoyine da babu irinsa a duniya.....zabin da a yanzun zata iya daga hannu ta gayawa duniya NAGARTACCEN ZABI NE. Zabi ne mafi sanin ciwon diya mace....mafi iya tausayawa da tausasawa cikin mu'amalarsa. Bai ko waiwayi sashensa ba,ya wuce kai tsaye zuwa ga sassan nanay. Da confidence dinsa,ya saba tun a baya,duk inda yaje ya dawo sassan nanay shine guri na farko da yake fara saka qafarsa don tasan da dawowarsa,to yau dinma sai yakejin bashi da wani haufi ko fassara da nanay zata masa,don ba baqon abu bane zaiyi. Cikin girmamawa dukkan hadiman ke zubewa suna gaidashi,har ya iso babban parlor din dake dab da sassan dakunanta. Babbar jakadiyarta ce ta iso,ta zube tana miqa gaisuwa. "Allah yaja da ran yarima.....yarima mazan fama.....zaki kuma dodon masu laifi" Murmushi ya danyi,matar tana cikin amintattu mafi dadewa cikin masarautar da suka jima tare da nanay. "Barkanki.....nanay fa?" Ya tambaya yana duban lokaci. "Tana ciki...ayi maka iso ne?" Kai ya gyada a hankali. Bayason shiga kai tsaye nanay din ta masa wata fassarar,don haka yayi zaune yana jiran dawowarta. *zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 08187255862 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 08187255862 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 86* ____________________________ *_Amintaccen gurin siyayya_* *_ingantattun kaya akan ingantaccen farashin da ba irinsa a kasuwa_* *_BONONZA DA PROMO akai akai_* *dukka sai a HUGUMA CLOSET* *Duniyar kayan yara,mata,maza,dukka* *shaddodi,atamfofi,laces,abayas,jakankuna,takalma,agogo,sarqoqi,English wears,night wears,under wears,da duk wani nau'in sutura babba da qarami* *_Karki yadda ayi babu ke.....leqa kiga yadda closet din HUGUMA kullum ke cike da kaya akan farashi me kama da KYAUTA_* *_YAN SARI....YAN REPOSTING.....DA SARAKAN ADO MASU SIYA DON KANSU....DUKKA INA MUKU MARABA_*🤝🤝🤝🤝 https://chat.whatsapp.com/FrqgC0YmUWP4FPmUzYuLJX ___________________________ Kafin kowa a cikinsu ya sake cewa komai bayan shurun,jakadiyar ta nema iznin shigowa. "Qaraso hawwa" Nanay ta fadi tana gyara zamanta. "Yarima haisam ne ya qaraso......yana zaman jiran ganinki" Dubanta sosai nanay tayi,kafin a hankali tace "Kina ganin ya cancanci ganina yanzu?....kice ina masa barka da dawowa.......zai iya tafiya saida safe,bazam samu fitowa ba,ina da mara lafiya" Ta fadi sannan ta dauke kanta tana maidawa ga akhnan. Taji komai,amma tayi kamar bata jiba,taci gaba da juya fruit din cikin bowl din. Miqewa jakadiya hawwa tayi tana ficewa a nutse. Idanunsa ya lumshe sanda take isar masa da saqon har ta kammala,ta kumaci gaba da zama tana jiran jin abinda zaice. Kamar bazai magantu ba saboda wani matsewa da zuciyarsa takeyi,ya tabbata dai ta dauke masa akhnan ne,kuma tunda ta hanashi ganinta yasan tabbas wannan horon da wannan hukuncin takeson masa. "Ki shaida mata,alfarma daya ta gaisuwa kawai" Ya fada a hankali. Qasa da kanta jakadiya hawwa tayi,sannan ta miqe da girmamawa tana komawa. Shuru nanay tayi tana saurarenta har ta kammala. "Baki gaya masa ina da mara lafiya ba?" "Na shaida masa ranki ya dade" "To ki sake jaddada masa hakan.....bana buqatar qarin aike kuma" "In sha Allah" Ta fada tana miqewa. Waiwayowar da nanay tayi shi ya sanyata saurin sadda kanta qasa tana latsa wayarta da noorah ta miqo mata tace ana kiranta. Zuciyarta na bugawa a hankali a hankali,fatanta kada nanay ta karanci komai cikin idanunta,fatanta nanay bataga komai ba. Murmushi ne kawai ya qwacewa nanay can qasan zuciyarta,irin wanda ko a saman fuska baya nunawa. Zata barta akan bata ganta ba.....amma yanayin ya mata dadi sosai. "Allah yasa su zamewa junansu sanyin idaniya" Abinda ta furta kenan sannan ta miqe a nutse. "Zansa a tura miki Aanani,kamar akwai abinda kikace kinason tambayarta ko?" Kai ta gyada a hankali ba tare data iya dagowa ta dubeta ba,don sosai gabanta yake faduwa na hada idanun da sukayi da nanay. A nutse nanay ta juya ta fita,ba taqi zuwa ganinsa bane saboda wani laifi ba,aah....idan akwai laifin ma daya ne,na kasa daga qafa yayi haquri da kwanaki ukun da suka rage. Ta kasa zuwa ne saboda ita kanta kunyarsa takeji. Wannan yaron data haifa ta riqeshi tsakanin hannuwanta ta raina a yau har yasan wata diya mace?. Idan ta tuna ita kanta kunyar hakan takeji. Siririyar ajiyar zuciya ta sauke sanda taji fitar nanay. Tana jin maganan noorah sama sama dake bata labarin walimar da hussam zaiyi a gobe ta bikin aurensu da walimar nanay dinma da za'ayi washegari. Ba duka hankalinta ke kan yarinayar ba,hankalinta yana can......can parlor din da haisam yayi aike har sau biyu wa nanay taqi kula da buqatarsa. Haka kawai taji tausayinsa ya sauka a zuciyarta. Indai batun gaskiya zata fada.....ba shakka yana da haqurin da a gurare qalilan ta taba ganin fushinsa da fadansa. Yana da kawaicin da ba'a kan komai yake daga idanu ya kalleka ba bare ya nuna yasan abunda kayi masa. Saita sauke ajiyar zuciya tana jawo daya wayartata ta kunnata,don bata lura tun safe a kashe take ba,daidai sannan saqonshi na dazu ya fado. Na farkon ta fara dubawa,sannan ta tafi na biyu da yake cewa. *_I have been in meetings for hours… and somehow you are still distracting my mind._* *Did you rest?* Wani murmushi ya subuce mata a hankali,kyawawan labbanta suka motsa. A hankali taji kalaman suna melting zuciyarta,wani tausayinsa ya taso yana danneta. Sai taji kaman taje ta roqi nanay ta ganshi.....sai taji kaman ta tashi taje ta bashi haquri,sai taji kuma tana hucewa daga jin haushi da tunanin shine ya turo mata nanay. Saidai me?,tana bude idanunta saita tsinci nanay a tsaye a kanta,da alama tayita sallama ne bataji ba. "Tunanin me kike haka?" Ta fada tana sunkuya ta dauki muqullin data bari a gefanta. Da sauri ta kifa fuskar wayar,ta kuma kasa cewa nanay komai harta dauki keys din ta fice. Tana sake daga fuskar wayar saqo ya shigo mata ta WhatsApp. Bata fiya hawanshi ba,amma yanzun sunan shehnaz ta gani,don haka tayi clicking da sauri tana budewa. Wani faffadar banner ne me matuqar girma da kyau,wanda ke dauke da sunan MAISON AKHNAN. Basai tayi tambaya ba,don daga gefe akwai qananun rubutun dake gaya mata. Wannan kamfanin da tafi amfani tafi kuma qaunar turarensa sama da kowanne turare.....sune zasu bude sabon kamfaninsu a dubai. A qasan banner din rubutu shehnaz ta aiko mata da harshen French. (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) "Da alama wannan grand opening din saidai mu gane miki shi.....saura kwana biyar kawai....zai barki?" Idanunta ta lumshe tana jinta tana dan rikicewa. Taci burin zuwa dubai....taci burin zuwa wannan taron,taci burin zuwa kamfanin ko zata samu ta gana da shugaban,ko zai mata alfarmar siyar mata da wannan qamshin. Qamshin da a yanxi takejin ya zama ruhi da zuciyarta sama da yadda take jinsa a baya. Tanaso ta bashi mamaki ta mallaki qamshin ba tare da yasan a inda ta samoshi ba. "Zanyi addu'a shehnaz.....idan ina da rabo,ko ba yanzu ba....ko bayan taron zanje". Voice note shehnaz ta aike mata dashi,wanda dariya ce zalla ciki da tsokana har tana cewa. "Me yasa wannan princess din tamu ta zama me laushi haka cikin qanqanin lokaci?" Murmushi kawai tayi,saima ta kashe data ta sauka,don ba zata biyewa shehnaz ba. Abu daya ta sani,komai a rayuwa yana da lokacinsa,komai kuma ba zaka taba gane anihinsa ba idan baizo kanka ba. Ya tafin kamar yadda nanay ta aiko masa. Saidai tun kafin ya qarasa sashensa yayi aiken neman izinin ganin motii a daren. A ransa yakejin saidai nanay ta masa haquri kawai wannan karon. Toilet ya shiga yayi wanka,sannan ya fito ya shirya cikin Moroccan thobe baqa data haska fatarsa ta sake fidda kwarjini da wani kwantaccen kyau da yawa yawan qabilar Ethiopian oromo suke dashi. Ya zura flip flops dinsa masu taushi yana kurbar tea din da yau gaba daya shi da dabino kawai ya iya ci. Yana jin kamar za'a rabashi da wani.mafi girma da kimar abinda ya taba mallaka a rayuwarsa ne. Qarar wayarsa ya dakatar dashi daga shirin fitar da yake. Ya koma ya dauka yana ganin sunan abbool yana yawo. "Uhmmm" Yace masa yana maqale wayar a kunnensa. "Akwai jet da zai iya tashi dakai qarfe takwas na daren gobe zuwa dubai din......na gama magana da ma'aikatanmu na can,sun kammala shirin tarbarka" "Good job abbool......ka yiwa hussam magana ya saka maka dollar dubu biyu a account dinka ladan aikin da kayimin cikin sauri" Wani farinciki ya ballewa abbool din,har yana nunawa a muryarsa. Aiki da mai gidan nasu komai qanqantarsa riba ne dashi,ballantana shi din,mutum ne da yake very serious akan komai nasa,shi yasa muddin zaka zama serious akan kowanne aiki naka taku zata yita zuwa daya. Ya rusuna duk da baya ganinsa ya fara masa godiya....godiyar da bai tsaya ya qarasa saurarenta ba ya datse kiran ya ajiye wayar yana wucewa gurin motii. Sassanyar iska ce take kadawa a kowanne sashe na gidan. Iskar dake sake kashe masa jiki da saukar masa da wata sabuwar kasala. Dukkan hadimai kowa yana kan aikinsa da wani irin tsari da qwarewa da cikakken horon da suka riga suka samu kuma suka saba dashi daga gurinsa. Duk inda ya gifta hadimai ne suke zubewa suna gaidashi cikin girmamawa,shi kuma yana amsasu cikin nutsuwarnan tasa da zai wahala ka rasata a tare dashi. Iska ya zuqa sosai ya fesar daga bakinsa yana duban gidan yadda ya soma yin fayau saboda shigowar dare. Ta yaya zai iya kwana shi kadai yanzun?. Ta yaya zai fara fuskantar wannan yanayin?. Bazai iya ba,bayajin zai iya karbar wannan sabon yanayin.....wannan kadaicin. Ta yaya zai iya shiga dakin ya kwanta shi kadai,me yasa nanay ba zata fahimceshi ba?. Kai tsaye yake takawa cikin babban bangaren motii dake da wani tsaro da tsari. Tsaron da komai aka tsarashi akan na'ura dake kula da motsin kowa da isowar baqi. Wani irin katafaren gini me matuqar tsari da daukan hankali,shuru sashen yake a hankali har ya qarasa qofar madaidaicin dakin da aka qawata da wasu irin manyan filalluka masu fibers dake dauke da tamburan da zane na gidan sarauta. Yana zaune saman lallausar daddumar ruwan madara,hannunsa riqe da carbi. Ya sukuya a hankali yana zare takalmin qafarsa bakinsa dauke da sallama yana takawa zuwa saman abun sallar. *_to nanay dai uhmmmm......da alama qara za'a kaiki kenan😂😂_* *_Satin nan da zamu shiga Monday kenan in sha Allah,kowa ya shirya,satin saukar alkhairai ne in sha Allah💃🏽💃🏽💃🏽💃🏽_* *_Abubuwa kala kala......sai kowa ya zama cikin shiri_*🙏🏽🙏🏽😄 Asha weekend lafiya Huguma na muku fatan alkhairi *zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 08187255862 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 08187255862 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 87* _________________________ https://chat.whatsapp.com/BkfPzSEDhnsIwyCD8LNGkm?s=cl&p=a&mlu=0 *IDAN KINSAN BA ORDER DIN KAYA ZAKI DINGA SAKAWA BA* *IDAN KINSAN BA BUSINESS KIKE DA NIYYAN YI NA KAWO KAYA DAGA CHINA BA KARKI SHIGA* *_DON ALLAH KARKI BATAWA KANKI LOKACI_* *_Assalamu alaikum my loyal people_* *_Barkanmu da wannan lokaci,kuma barkanmu da warhaka_* *_akwai da dama cikin mata wadanda suke sha'awar yin order kaya daga CHINA zuwa NIGERIA,NIJER,CAMERON,CHAD da GHANA_* *_Amma rashin samun amintaccen company....ko hannun wanda zasu dinga siyan kaya ta hannunsu cikin aminci ya hanasu_* *_To a yau addu'ar da yawa daga cikinku ta amsu,don nayo muku tsarabar kamfanin da zakuyi siyayya ta hannunsu su kuma dora muku kayanku har qasarku cikin aminci ba tare da fargaba ko d'ar d'ar ba_* *_kunsan komai nawa TASTED AND TRUSTED ne,to wannan kamfanin idan akwai abinda yafi TASTED AND TRUSTED ma shine_* *_Baki da fargaba kota sisin kwabo,ni SAFIYYA HUGUMA na tabbatar da hakan_* *_Zaki iya kasancewa dasu group nasu,inda a nan zaki hadu da agent dinsu da CEO nasu gaba daya ta wannan link din,zaki samu bayanansu da komai da ya shafi mu'amala dasu_* *INA ME BAKU TABBACIN AMINCI DA INGANCI DA SAUQIN MU'AMALA DASU DA IZININ ALLAH,BAN TALLATA MUKU SU BA SAI DANA GWADA* *Allah ya dafa mana,yasa mana albarka a nemanmu,ya albarkaci halal dinmu ameen summa amee* _________________________ A nutse ya zauna cikin nutsuwa da girmamawa,idanunsa a rusune gaban moti aba jifar. Cikakken dattijo,tun daga halayya zuwa kammni da dabi'unsa gaba daya. Adalin sarki kuma jagora da al'ummar qasar jimma ke ji dashi. Zabgege dashi me zubi da surar qabilar oromo ta anihi. Yana da wani irin kyau wanda akasan yawa yawan qabilun qasar habasha dashi,akwai wasu kammanni kadan nashi da wasu daga cikinsu Anaani da suke debo. Tare suka shafa addu'ar da ya kammala shi da haisam din. Idanunsa akan haisam,fuskarsa dauke da murmushin da zallar sabo yake nunawa muraran. "Barka da warhaka abuu" Ya furta cikin girmamawa da rusunawa yana kiranshi da sunan da su kadai ke kiranshi dashi. "Barka kade muhammad......sannu da qoqari" Motii din ya fadi. Yasan aikin daya tafi yi addis ababa,don ba inda zaije ya boyewa motii din bai sani ba. Kusan duk wani gwagwarmaya da zai shiga yana iya boyewa nanay,saboda ita din uwa ce,tana da tarin rauni da abubuwan da ba zata iya jurar taji ko ta gani tattare da yaronta ba. Zata iya damuwa ko ta saka damuwa cikin ranta,amma motii kuwa jajirtaccen uba ne da kusan qashin bayan nasararsa shine. A komai yana iya riqe masa hannu. A komai yana dafa masa da dukkan iyawarsa. "Yauwa motii......fatan na sameku lafiya" "Alhamdulillah......amma......wanne irin sauqi aikin yazo dashi haka naga harka dawo qasa da lokacin da kace?" Motii ya fada yana kallon agogo gami da jawo wani irin mazubi da akayi mixing gargajiya da zamani wajen qerashi. Wani irin mazubi ne dake nuna zallar iko da daukan hankali,kamar an sassaqashi ko kuma qerashi akayi. Qasa ya danyi da kansa yana rasa abinda zaice masa. Wani sashe na zuciyarsa na shawartarsa yakai qorafinsa kawai. Idan ance anfi sabawa da shaquwa da uwa......shikam zaice tsakanin motii da nanay bazai iya zaban daya yabar daya ba. Kowanne a cikinsu akwai kalar sabo da shaquwar dake tsakaninsu,kowanne akwai kalar wani sirri da yake tsakaninsa ne kawai dashi,kowanne akwai kalar maganganun da suke iya tsakaninsu ne. "Na barwa bobbo ragowan zai qarasa.......tafiyata dubai ne ya taso motii" Yayi maganan yana yin qasa da kanshi. "Ma sha Allah.....ma sha Allah" Ya fadi da murmushi bayan ya bude mazubin gabansa. Lafiyayyen nono ne da aka zuba masa wani abu me kama da fura sannan aka bishi da sauran kayan itatuwa irin inibi da sauransu. Ya saka ludayin masu kyau na wata irin tasa dake kama da azurfa daya a gabansa daya a gaban haisam din. "Lokacin yayi ne?.....kamar nine banyi lissafin daidai ba kenan?" Murmushi kadan haisam yayi yana girgiza kai,bayan ya saka hannu ya dauki ludayin. Bawai don yana da niyyar sha ba,....don tun sanda ya tabbatar ba akhnan a sassansa komai ya daina masa d'an d'ano. "Ya Allah.....kada ka sanya jarrabawata makauniyar soyayya ce" Abu na farko daya fara roqon Allah kenan. Ya sani,tun ba yau ba,yana da wani irin hali na so me matuqar girma da qarfi ga duk abinda yakeso. Koda dabba ce yake kiwonta,to zai mata so na gaske,wannan ya sanya bai bata saida dokinsa ko raqumi ba,saidai ciwo da ajali ya rabasu dashi. Yadda yakeji yanzu a kanta,awanni kadan da bata gefansa sai yakejinsa wani uncompleted. "Baka lissafa ba daidai ba motii......kawai inaso nan da gobe ko jibi na fara yin gaba saboda ragowar shirye shirye. Zan shiga masarautar dubai din......sarki mohammad bin rasheed Almakhtoum,akwai wasu royal distribution rights da zan karba daga gurin prince Hamdan bin muhammad Almakhtoum.....still akwai wasu papers da zan kammala concerning na kamfanin......bayan haka mun samu mutane da yawa da sukeso su saka hannun jarinsu a ciki,akwai buqatar mu tattauna dasu. Ba dubai emirate kawai ba......akwai Emirates da kusan hudu da sukeson turarukan da zamu fara fitarwa saboda masarautunsu da royal events nasu" Kai kawai motii yake jinjinawa. Shi kansa ya sani,wata baiwa ce Allah S W T ya sallada shi zai haifeta. Wata irin tarin baiwa ce da Allah ya qaddara ta jininsa zata fito. Muhammad haisam.....shi ya haifeshi,amma shi kansa yasan cewa wata ajiyar Allah ce yaron. Nasararsa ta girmi shekarunsa. Baiwarsa da hikimarsa ta d'ara shekarun da yayi a duniya. Dashi da nanay dukka abu guda suke roqa masa MACE TA GARI,sunsani ita daya ce zata sama silar ci gaba da wanzuwarsa a yadda yake,ita daya ce zata tallafeshi ta bashi kafadunta a duk sanda yake buqatar hakan,ita daya ce zata bashi hannuwanta ya kama yaci gaba da tafiya a sanda ya laluba hannunsa cikin fadin duniya yaji WAYAM babu su a raye.....zai karye.....zai fadi qasa warwas.....zai rasa dukkan nasararsa a duk sanda ya rasa MACE TA GARI. "Allah yayi albarka Muhammad.....ga iyali ka fara ajiyewa......wadannan hidimomin....karka yarda su hanata lokacinka" Murmushi ya saki me sanyi,wannan kalar murmushin da ko yaushe yake cakude da nutsuwarsa. Yana jin motii ya soma sosa masa inda yake masa qaiqayi. "In sha Allah abu" Ya fada da girmamawa. "Amma da iyalinka zaka tafi ko?,kasan ba wani abu da zai gagari mutum.....ba wata gajiya da zata da yiwa d'a namiji tasiri me yawa idan akwai mace a gefansa" . Wani irin sanyi da dadi yaji yana ratsashi. "Barakallahu fi umrik" Kawai yake maimaitawa a ransa yana yiwa motii addu'a da fatan alkhairi. "Zanso hakan motii" Ya fada da murya can qasa yana saukar da kanshi qasa. Dakatawa kadan motii yayi yana duban fuskarsa,daga yadda yaga yayin yasan akwai magana ne cikin ransa,fada ne baiyi ba,kaman yadda yake da kara da yakana a lokuta da dama. "Tunda kanaso.....me zai hanaka tafiya da matarka?" Maganan ya masa nauyin daya sake shafa sumarsa. Ta ina zai fara?,yace nanay ta dauketa saboda ya raya sunnah da matarsa?,ko kuma meye?. "Tana gurin nanay" Ya furta a hankali kansa a qasa. Shuru motii kawai yayi yana kafe haisamd din da kallo. "Tama gurin ta?,bata barta tayi jinyartaka ba kenan?" Motii ya masa tambayar da haisam din yaji kaman yana nutsewa a gurin. "Tayi" Ya amsa masa kawai a taqaice. Bayaso ya qara komai,bayaso ya sake cewa komai,gani yake komai da zai sake fada kaman zai tona asirinsa ne. Shuru da wani irin idanun nazari motii ya zubawa haisam din,yanason nazartar komai Koda yaron nasa bai gaya masa ba. Na wasu sakanni kawai wani boyayyen murmushi ya subucewa motii din. Can qasan ransa yaji kaman ya karanto komai a sunkuyayyen kan haisam daya kasa dagashi. Shi bai taba ganin rigima irin ta nanay ba,hasalima baisan matarsa rigimammiya bace sai yanzu. Baisan wanne irin so takewa surukartata ba,har idanunta suka rufe tana son illata d'anta?. "Motii yana kiranki,idan zai yuwu kada yayi sama da minti goma" Abinda kunnuwan haisam suka jiye masa kenan,sai ya daga kansa a hankali yana saukewa akan motii daya ajiye wayar a gefansa. Sai a sannan ya fahimci nanay ya kira,ya danyi rau rau da idanunsa,da wannan yanayin da yakanyi a gaban iyayensa.....wannan yanayin da a gaban mutum biyu kawai yake bayyanashi RAUNINSA. Sai a yanzun da Akhnan ta zama ta uku.....ta ukun da a yanzun tayi wani juyi zuwa ta farkon da tasan rauninsa sama da kowa. "Abu.....karfa taga kaman na kawo qararta ne". Daga kansa motii yayi yana dubansa sosai. Murmushi ya saki yana juya nonon "Lallaba maka ita zanyi,ni kaina bani da qarfin fada da khadeeja ai". Murmushi yaso qwacewa haisam,wannan soyayyar,....wannan qaunar na daya daga cikin abubuwan da idanunsa suke kalla suke kuma matuqar burgeshi. Dukkan power da ikon fada aji motii nada shi saman nanay. Ba wani umarni da take tsantsan bi irin na motii,ba wani umarni da take gaza tsallakeshi irin na motii. Amma motii din ya bata wani irin 'yanci dama da kuma sakewa. (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) Wannan sakewar sabanin ta matan yanzu ce. Wannan sakewar bata sanya nanay tanayin abubuwa marasa kyau ba ko abubuwan da taga dama ba. Ta riqeta ta hanya me kyau da yin komai daya dace,wannan ya sanya motii din ya sake sakar mata sosai. (Qalubale ga matan da Allah ya bawa dama a gidan miji,kiyi abinda ya dace a sanda ya dace da damar da miji ya sakar miki,kada kisa son ranki ko rashin tsoron Allah a wannan damar da kika samu,idan kika sanya hakan sai Allah ya qwace abarsa). "Kasha muhammad" Ya fada yana sake tura kwanon gabansu. Yasha daya biyu motsin nanay ya tunkarosu,sassanyan qamshin nan nata na dindindin na turarukan shuwa incense and more,wani qamshi da ya zama signature dinta musamman da dare irin haka idan zata kasance da motii din (Shuwa incense and more +234 704 229 3387). Yana ganin yadda ta bata fuska sanda ta sanya idanunta akan haisam din. Sai ya sunkuyar da kansa dukka nauyin duniya yana saukar masa. Sai a lokacin ya sake tuna yadda yabar gadon,kamar ya nuna akwai staining na jini guri guri,kuma duk ta gani?,ya tambayi kansa. Sama sama ta amsa yadda yake gaidata,ta kuma zarce zuwa gefan motii tana zama kusa dashi da wani zama me nuna tsantsar ladabi. Wannan zaman ya jima yana ganin tana yinsa.....a gaban motii kawai,banda gabansa baiga tana yinsa gaban kowa ba. Zaman yana burgesbi,a tarin shekarun da sukayi dashi bata sauya zama a gabansa ko daya "Gani ranka ya dade" Ta fada tana sake tsuke girarta,sai haisam ya miqe cak zai tashi. "Koma ka zauna" Motii ya fada yana boye dariyarsa. Komawa yayi d'an nesa dasu kadan ya zauna yana cusa yatsunsa cikin lallausar sumarsa kafin ya zaresu yana yin qasa da kansa. "Cewa nayi.....bari na nemawa yarona aron matarsa...." Yayi maganan yana duban tsakiyar idanun nanay din. "Aron matarsa" Taji kalmar ta mata banbarakwai a kunnuwa. Tasan motii,ba sanin jiya ko yau ba,ya fadi.maganan a haka ne saboda dama taji banbarakwai din. Ya fadeta a haka ne saboda ta gane abinda tayi bai hau kan tsari ba,ta yadda salin alin maganarsa zatayi tasiri ba tare daya fito ya fada ba. Bata dauke Akhnan haka kawai ba sai don saboda shi,amma kuma shi din bazai gane ba. Akwai abinda take jira daga Senegal,kuma sai gobe zai iso,da dare koda safe. Ba kuma zata bashi ita ba sai abun nan ya iso ta mata amfani dashi. Yadda take fatan ya mallake zuciyar matarsa......haka take fatan matarsa ta mallake zuciyarsa. Tanaso taga gidansa ya kasance ALJANNAR DUNIYA sama da gidan kowanne magidanci data sani. Akhnan da haisam tuwona maina ne,a cikin su batasan wa zataso ba.....wa zata bari?. "Qarata ya kawo maka kenan?" Ta fada cikin iya rigima irin tata da motii ne kawai ke fahimtar hakan. Murmushi ya maye gurbinsa da dariyar dakeson qwace masa. "Aah....ko kadan,yazo shaidamin zai wuce gurin bude kamfaninsa ne.....sai naga a yanzun ai ya zama magidanci,bai kamata ya tafi warin takalmi ba......wai wanne irin al'adace haka khadeeja da taqi qarewa?" Fuska ta dauke tana tsuke idanunta. "Laifi yayi" "Laifi?" Motii ya fada yana qin duban sashen da haisam dinma yake. "Eh" Ta fada tana sake tura fuskarta gefe daya ba tare data bari motii ya kalla ba. Murmushi ya qwacewa motii din bayan ya gama raba idanu tsakaninta da haisam din,sai ya saki murmushi yana sauke kansa qasa. "A duba mana to muna roqon alfarma" "Sai nayi shawara" Ta fada hankali kwance. Mamaki ya sake kama motii,ya waiwaya ga haisam yana cewa. "Jeka muhammad.....jeka abinka" Tsam haisam ya miqe. Satar kallon nanay yakeyi. Shi gani yake kaman nanay din ta sauya masa gaba daya,ta rage ji dashi,kwata kwata kaman ba ita ba. "Khadeeja......ki bashi matarsa......" Motii ya fada calmly yana duban fuskarta da sauran murmushi akan tasa fuskar. "Zan duba na gani" Ta sake fadi. Da gaske batason bashi akhnan yanxun,so samu ta gama sabon gyaran daya ballo mata. So take a duk sanda zai sake koma mata yaji kaman a ranar yake sake saninta a karo na farko a rayuwarsa,kaman yadda takeso akhnan din ta samu salama itama ta fara sanin dadi da ma'anar abun bawai wahalar kawai ba. "Ina guje miki halin d'an yau......haka na gaya miki wancan ranar baki yarda ba.....me ya biyo bayan nan?" Baki ta tura sosai tana duban motii. "Ni kam abuu.....kai kake goyon bayan yaron nan.....b'arna yayi kuma dole a gyarata. Yayi tafiyarsa shi kadai mana,idan yaje ya dawo ai dole na bashi abarsa ko?". " Allah ya bada sa'a" Ya fada kawai yana maida kwanonsa gabansa. Shi namiji ne,kuma ya fita sanin dawar garin. A yadda yake ganin idanuwan haisam ya tabbatar zai wahala bai sake shayar da ita mamaki ba,idan da rabon hakan kuma to shi mene nasa?. *zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 08187255862 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 08187255862 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 88* ________________________ *_Domin qulla huldar kasuwanci damu,HUGUMA CLOSET.......,siya ko siyowa wani,reposting ko sari akan farashi me rahusa da babu irinsa,maza yi joining group namu don samun ingantattun kayan da babu ha'inci a ciki da izinin Allah_* https://chat.whatsapp.com/FrqgC0YmUWP4FPmUzYuLJX ___________________________ *H A I S A M* A hankali ya rufe bangon littafin D'AUQUL HAMMAMAH(ring of the dove) da yake dubawa,littafin daya tattare dukkan wasu sirrika na sanin halayya da dabi'un mace na ainihi. Cikakken ma'anar soyayya,alamunta da yadda shi kansa son yake. Ba wannan bane karo na farko daya karanta littafin ba,zai iya cewa tun yana da shekara ashirin da daya a duniya ya karanta littafin,ya kuma maimaitashi shi da ire irensa da dama,wannan ya sanya ya tara wani irin sani da ilimi akan halayyar diya mace me yawan gaske. Yanason littafin,don kullum ya karantashi sabo yake jinsa,amma a yau sai yaji gaba daya littafin bai masa dadi yadda ya saba. Hasalima yaji yaji idanunsa ke masa,gajiyace kuma fal idanunsa,tunda ya dawo daga gurin motii ya shiga sassansa sai ya kasa zama,dole ya bulla ya koma library dinsa,saboda sanin da yayi cewa shine guri qwaya daya tal dake debe masa kewa komai yawanta. Amma a wannan daren......a wannan lokacin su kansu tarin litattafan sun gaza dauke masa komai. Ya riga ya tsara,ya kuma sanya a ransa a yau zaiyi bacci me yawa rungume da ita a jikinsa,amma cikin qanqanin lokaci nanay ya rushe wannan tsarin gaba daya. Ya sake murza idanunsa,baccin yakeji da gaske,amma babu ta yadda wannan baccin zai yuwu ya tabbatar. "I can't" Ya furta a hankali yana motsa labbansa,kawai sai ya ajiye littafin ba tare daya maidashi muhallinsa ba,ya zura flip-flops dinsa ya bude qofar da zata sadashi da sassansa. Kayan jikinsa ya zare,ya sauyasu zuwa wasu kalan cotton pajamas masu hasken launi. Ya matsa gaban dressing table dinsa ya sake feshe jikinsa da sassanyan turaren nan nasa,ya gyara sumarsa da comb ya fesa hair mist,bayan ya saka Beard perfume dinsa,na chest hair perfume sannan ya feshe bakinsa da wannan mouth fresh din nasa na mint dan amana. Wayoyinsa ya kashe yana ajiyesu nan,ya taka ya fara fita a dakin a nutse. *A K H N A N* Shurunta ya sanya dukkan wadanda ke dakin suka dauka bacci tayi suka fice,saidai kuma idanunta biyu,tana jin sanda nanay da kanta ta shigo ta dubata,ta kashe mata dukka fitilun dakin,ta rage mata Ac sannan ya maida hasken ceiling din zuwa dim light sannan ta fice. Numfashi taja sosai tana fesarwa. A wuninta daya tak a sashen,ta samu wata irin kulawa data kusa ninkin kulawar da take samu a agadez ta wata da watanni,amma kuma can cikin ranta....cikin cikin ruhinta da gangar jikinta tana jin wani irin emptiness. Can cikin zuciyarta da ruhinta tana jin wani abu kamar bai cika ba......can cikin naman zuciyarta takeji akwai wani abu da take KEWA. Tayi juyi da mutsu mutsu har batasan iya adadi ba,duka a qoqarin gyara kwanciyarta wai ko zata jita comfortable,kaman wannan yanayin da takeji kwanciyarce batayi daidai ba. At last ta gane muhallin ne baiyi daidai da gurin ba......a qarshe ta gane ba nan ne gurin da gangar jikinta yake buqata ba. "Haisam" Ta fadi sunan a hankali,saidai.kaman ana jiran ta furta sunan ne taji an buda qofar a hankali da wani irin yanayi da ba lallai ka lura ba idan ba hankalinka yana gurin ba. Bata tsorata ba......amma rashin zaton shigowar kowa cikin dakin a wannan lokacin yadan bata mamakin da yasa ta wara idanunta sosai ta qasan abun rufar tanason gane waye ya shigo?. Kwanyarta bata wahala ba.....tambayarta batayi nisan kiwo tana shawagi ba qamshin nan nasa ya gaya mata MUHAMMAD HAISAM NE. Wani abu ya buga tsakiyar zuciyarta,wani irin yanayi ya saukar mata a hankali,wani irin sanyi yana ratsata tun daga tafin qafarta zuwa saman kanta. Tunda ya tako qafafunsa cikin dakin,idanunsa suka sauka a kanta yakejin kamar wani magent ne yake jansa. Numfashinsa ya sauya da wani irin yanayi na bugun zuciya a sanda taga daya zuciyar 'yar uwarta. Ya shaqi qamshinta sosai,sabon qamshin da yakeji tattare da ita tun a wancan ranar data shigo hannun nanay dinsa zuwa yanzu. Idanunsa a kanta,ya sanya hannu yana balle dan maballan gaban rigarsa a kasalce Tana iya ganin motsinsa a tsaye,batasan me yakeyi ba,saidai koma meye din yakeyi ba abinda yake sanyawa zuciyarta sai wani matsanancin bugu da takeyi. Tsoro ke saukar mata a hankali,ya akayi cikin sauqi haka ya iya riskar dakin?. Baya tsoron wani ya shigo ya ganshi?,me ma ya kawoshi?" Ta yiwa kanta dukka wadannan tambayoyin. Tayi.shuru ne kawai ta dauke numfashinta,tana sanya ran ya koma inda ya fito yayi zaton bacci takeyi. A kasalance yake zare rigar jikinsa. Wani irin kwadayinta yakeyi,kwadayin wannan lallausar fatar me sulbi qamshi da taushi. Mahaukaciyar kewarta ce take taso masa,kamar tsohon zakin daya jima baiga abinci ba yaga nama. Har lumshewa idanuwansa sukeyi da kansu,ya kammala zare rigar sannan a hankali ya nufi gadon ya soma haurawa. "Me yake shirin yi haka?" Ta tambayi kanta zuciyarta tana bugawa,saidai duk da haka bata shirya fallasa masa kanta idanunta biyu ba,don haka ta maida idanunta ta lumshe. Tana fatan idan ya hawo saman gadon yaji bacci takeyi ya koma,saidai fatanta baici ba,don a hankali taji yana daga duvet din da take ciki,sannan ya fara zura jikinsa cikin duvet din yana hade tazarar dake tsakaninsu a hankali. A hankali ya mata kyakkyawan masauki cikin jikinsa,wata sassanyar runguma ta baya wadda faffadan qirjinsa ya laqume fadin bayanta gaba daya. Wani irin sauti zuciyarta ke bayarwa,tanaso ta miqe ta zare jikinta,ta masa magana ko ta hanashi,amma ta gaza aiwatar da ko daya daga ciki,sai zuwa sanda ta aza hannunsa saman ruwan cikinta ya jawota sosai cikin jikinsa yana sanya qafarsa daya tsakanin cinyoyinta yana rabasu. "Hah......hais......" Ta fadi a rarrabe ba tare data iya fadin cikakken sunan ba saboda yadda taji dumin cinyoyinsa cikin nata suna ratsata. "You can call my name my healer......amma bata irin wannan hanyar ba..... Qorafi......i hate complain akhnan pleeeeaaaaseee" Ya fada yana dan jan sunan sanda yake nutsar da fuskarsa tsakanin dogon wuyanta da gashinta dake a barbaje a gadon bayanta yana bada wani tattausan qamshin hair mist na kamfanin shuwa incense and more. "Barka da warhaka my princess......." Ya sake fada cikin wani irin maye kamar wanda yasha giya ya bugu. "I'm sorry biftu.....really sorry,for making you feel like i disappeared....i don't like how quite i left your day.......kiyimin afuwa" Shuru ya ratsa sai fitar numfashinsa kafin ya sake cewa. "......na karbi abu mafi girma da daraja da kowacce 'ya mace ke taqama da tutiya dashi......ya kamata na zama a kusa dake for the whole day....i'm so sorry my princess......" Ya qarashe da qyar saboda yadda numfashinsa yake nauyi a qirjinsa. "......next time i leave,you will know where i am and when I'll be back". (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) Shuru kawai tayi accent dinsa na kasheta.....shuru ta masa tana sauke numfashinta a hankali......shuru tayi tana jin yadda bugun zuciyarsa ke sauka a gadon bayanta.....shuru tayi tana jin yadda ya zura hannuwansa ta qasan rigarta ya soma yawo dasu a sassan jikinta. "I.......i......i know you didn’t mean it" Ta maida masa da French kaman yadda yayi mata muryarta tana rawa. "Thanks" Ya furta can qasan maqoshinsa. A hankali bugun numfashinsu ya sauya shi da ita gaba daya......a hankali wani abu ya soma yawo cikin jininta dama sassan jikinta,wani abu me nauyi da wani irin qarfi dake ratsa zuciyarta da kowanne sashe na jikinta. Saidai duk da haka.....duk da haka jiya bata fita a kanta ba.....wannan azabar......wannan wahalar.....wannan tsoron yana kwance cikin rai da zuciyarta. Bata manta ba......bata manta komai ba.....bata manta kowanne wucewar daqiqa minti da second ba.....bata manta yadda ya cillata wata nahiya me cike da azaba da radadi ba,don haka a yanzu jikinta yana kakkarwa ta sanya hannu ta damqe hannunsa da taji ya fara tafiya zuwa qirjinta kai tsaye da wani irin zafin nama da jikinsa yake gwada mata. "Babyyy" Ya furta a karon farko a hargitse. "Ba abinda zan miki.....just want to feel them......nayi missing......mayi missing nasu,bazan iya bacci bane ni kadai......don Allah......karki hanani,zan miki kuka" Yadda muryarsa ta narke.....yadda muryarsa ke rawa sai taji kaman kukan yake shirin sakar mata,abinda ya sake gigitata kenan. Tsoro takeji,sosai takejin tsoro biyu yana hade mata. ".....idan nanay ta shigo fa?" Ta fada itama tata muryar tana rawa. "Babe......Ki daina saka ni jin kamar zan ji tsoron mamana a gaban matata......" Ya fada yana qanqameta cikin jikinsa,bai kuma bata second chance da zatayi tunanin komai ba ya birkitota suka koma fuskantar juna. Yatsansa ya dora daga saman goshinta yana saukowa dashi zuwa karan hancinta,sannan ya wuce saman labbanta dake daukan hankalinsa,fuskarta ya kama ya saka tasa sosai a ciki,sannan ya zame fuskar tasa zuwa kan kafadarta,ya lalubi kunnenta,cikin wani narkakken yanayi ya rada mata. "Let me have this moment with my wife in peace.....no nanay tonight......only khadeeja and muhammad" Ya qarasa fada yana sake bata muhalli me kyau cikin faffadan qirjinsa. Numfashinsu.....shauqinsu......dama zuciyoyinsu gaba daya sukayi wani irin cakudewa guri daya cikin daren. Wani irin hot romance......zafafan saqonni daya birkita mata kwanya dasu......wani irin yanayi daya sanyata ta yarda cikakkiyar maqaryaciya ce ita data dauka zata iya bacci me dadi da ma'ana alhalin baya gefanta......alhalin baya tare da ita. Ya tarawa zucuyarta da gangar jikinta gaba daya gajiya. Ya aike da ita can wata qololuwar duniya da zata iya fadi kai tsaye a yau karon farko takai can din a yanayin da take cikin hankalinta. Saidai ya kauda mata kowanne tsoro ta hanyar cika mata alqawari. Yayi controlling din kansa,yayi namijin qoqarin dakatawa baikai har can headquarter din ba,ya jata a jikinsa cikin taushi da nutsuwa,wanda sai saukar numfashinsa taji a hankali kansa na kwace cikin qirjinta,yayi pillow dash yadda yakeso. Wannan tsoron ta dauka zai haneta sakewa......sai gashi ta manta da komai,wani daddadan bacci ya sureta yayi awon gaba da ita. *zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 08187255862 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 08187255862 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽 💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 89* __________________________ https://chat.whatsapp.com/BkfPzSEDhnsIwyCD8LNGkm?s=cl&p=a&mlu=0 *IDAN KINSAN BA ORDER DIN KAYA ZAKI DINGA SAKAWA BA* *IDAN KINSAN BA BUSINESS KIKE DA NIYYAN YI NA KAWO KAYA DAGA CHINA BA KARKI SHIGA* *_DON ALLAH KARKI BATAWA KANKI LOKACI_* *_Assalamu alaikum my loyal people_* *_Barkanmu da wannan lokaci,kuma barkanmu da warhaka_* *_akwai da dama cikin mata wadanda suke sha'awar yin order kaya daga CHINA zuwa NIGERIA,NIJER,CAMERON,CHAD da GHANA_* *_Amma rashin samun amintaccen company....ko hannun wanda zasu dinga siyan kaya ta hannunsu cikin aminci ya hanasu_* *_To a yau addu'ar da yawa daga cikinku ta amsu,don nayo muku tsarabar kamfanin da zakuyi siyayya ta hannunsu su kuma dora muku kayanku har qasarku cikin aminci ba tare da fargaba ko d'ar d'ar ba_* *_kunsan komai nawa TASTED AND TRUSTED ne,to wannan kamfanin idan akwai abinda yafi TASTED AND TRUSTED ma shine_* *_Baki da fargaba kota sisin kwabo,ni SAFIYYA HUGUMA na tabbatar da hakan_* *_Zaki iya kasancewa dasu group nasu,inda a nan zaki hadu da agent dinsu da CEO nasu gaba daya ta wannan link din,zaki samu bayanansu da komai da ya shafi mu'amala dasu_* *INA ME BAKU TABBACIN AMINCI DA INGANCI DA SAUQIN MU'AMALA DASU DA IZININ ALLAH,BAN TALLATA MUKU SU BA SAI DANA GWADA* *Allah ya dafa mana,yasa mana albarka a nemanmu,ya albarkaci halal dinmu ameen summa amee* _______________________ *A S U B A H* Sanye da fararen kayan sallah take takowa zuwa dakin a nutse don tayar da akhnan salla,kaman yadda ya zame mata al'ada tayar da kowa tsakanin Aareef rumaisa Aanani noorah da saamee. A nutse ta murda qofar dakin ta kuma turata a hankali tana shiga,saidai abu na farko data fara ji shine,wannan scent din da mutum daya ta sani ya mallakeshi. Ta bude hancinta a hankali tana sake shaqar qamshin don ta tabbatar. Shi dinne dai,ta miqa hannu tana kunna qwan dakin bakinta dauke da sallama gami da kiran sunan akhnan din da GIIFTII. Ba kowa saman gadon,tabi shimfidar gadon da kallo a hankali. Komai a yamutse yake,wasu pillows din sun fado qasa sun zube daga gefe. Idanunta ta dauke a hankali,wannan gadon bai kama da mutum daya bane kawai ya kwanta,yanayinsa kamar anyi dambe ko yara ne sukayi bacci akai suka tashi. Idanunta ta maida qofar bandaki sanda take budewa. Akhnan ce,sanye da doguwar riga cotton me laushi sosai data saukar mata har qasa. Ta sani,bada rigar ta kwanta bacci ba,kaman yadda gashinta ke a hargitse ba kaman yadda ta ganshi dazu data shigo ta kashe mata wuta ba. Qasa akhnan tayi da idanunta,haka kawai tana jin wani faduwar gaba dakunya suna saukar mata. Gani take kaman nanay tana ganin komai,yadda ya kwana tsakanin qirjinta,yadda ta farka fuskarya saman lallausan gashin kansa,yadda ta sake bude idanu ta tarara yana tsaye yana qare mata kallo,sumarsa na digar da ruwan da take da tabbacin wankan ibada yayi. Ya yarfa mata ragowar ruwan hannun nasa a tausashe yana sakin lallausan murmushi. Ta bashi wani abu da ake kira da suna NUTSUWA wato peace inji bature. A yau yasan yayi wani irin bacci daya amsa sunansa,kalar baccin da bai taba irinsa ba kaf rayuwarsa. "Gate up......ko kina so nanay tazo ta sameki a haka?" Duvet din data boye fuskarta ta janye kadan,tanason dubansa amma ta kasa,ta ganta a haka kaman yaya?. Daga ido tayi karo na biyu,caraf ya riqe idanun cikin nasa,ya mata nuni kuma da jikinta,takai hannunta a hankali tana tabawa. Ya rabata da komai sai a sannan ta tuna,ta cure guri daya tana duba lokaci,shirye shiryen sallar asuba akeyi. "Ruwan wanka yana ciki yana jiranki". " Ni bazanyi wanka ba" Ta fada tana tura baki kunya kaman ta kasheta. Karon farko ra yuwarta da taji sautin siririyar dariyarsa,ya tako a nutse yana isowa dab da kanta ya sunkuya kadan. "Ba zaki wanka ba.....amma awannin dazu kike fadin....." Sai ya sassauta muryarsa yana maimaita mata maganganun da ko daya a ciki ba wanda tasan tayi. "Wayyo Allah na bappi.....zai lalatamin kunnuwa na" Ta fada da siririyar muryar nan tata dake kasheshi,musamman duk sanda tayi magana da sautin shagwaba. Baya yaja a hankali sautin siririyar dariyarsa yana fita,wani abu daya zowa akhnan da wani sabon yanayi. "Ba sharri na miki ba,pillows din dake nan da suna magana zasu fada" "Nidai ka fita" Ta fada hawaye na tarar mata a idanu. Ya akayi ta bari ya yaudareta har haka yaji wadannan kalaman a bakinta?. Banda tasan baya qarya zata iya tsinewa kanta ita ba ita ta fada ba. Yana sakin qasaitaccen murmushin nan nasa dake gaya mata,ba abinda ta furta kawai ba......tuna komai daya shude cikin awannin dadi yake masa,ya koma private musallah din,ya shimfida tattausar daddauma ya tayar da salla abinsa hankali kwance,kaman baya duban lokaci,kaman baya tsoron wani ya shigo ya ganshi. Tayar da sallarsa ya bata cikakken daman wucewa bathroom din kai tsaye a gurguje,ta samu ya hada mata komai,hatta da towel da zatayi amfani dashi,kaman yadda birra ke mata. Sanda ta fito taga dakin wayam,batasan sanda ya fita ba,sai ta sauya kayanta kawai wanda tana kammalawa ta koma bandakin don daura alwala,fitowarta ne a yanzun sukayi kacibus da nanay. Idanunta kawai ta janye nanay din,jikinta yana bata akwai wani abu da yake ba daidai ba,saidai bata nunawa akhnan din komai ba tace "Alhamdulillah,kin tashi kenan". "Eh na tashi" Ta amsawa nanay wadda har takai bakin qofa a sannan. "Zenebe zata shigo zata ganki" Abinda tace kawai kenan tana fita daga dakin. Kawai juya abun take cikin ranta,tana tafe tana amsa gaisuwar hadimai da ma'aikatanta cikin girmamawa kaman yadda ta saba. Can qasan ranta take maido da yanayin dakin da qamshin haisam da taji,kadafa su bata kunya.....karfa ya sake maimaita wani abun kamar yadda motii ke fada mata. "Bayan na kwanta,akwai wanda aka sake budewa sassan nan ne?" Ta tambayi saamiyaa wadda keda alhakin kula da shige da fice na cikin dare. Qasa kadan tayi da kanta,tana jin nauyin fade,duk da ya wuce abinsa ne kai tsaye bayan ya tambayeta nanay din ta kwanta?,ba tare da yace mata komai ba. "Saamiya" Ta kira sunanta tana juya daffaffiyar madarar hannunta. "Eh......yarima haisam ne ranki ya dade" Shuru nanay tayi,ta gyada kai a hankali,kawai sai taji dariya nason qwace mata. Karo na farko......karo na farko kenan data taba shata iyaka da layi akan abu amma haisam ya tsallake. Ta yarda da maganan motii,ta kuma yarda duk wanda ya rigaka kwana zai rigaka tashi. Namiji baida amana akan mace da gaske ne,kota yaya ne zai samawa kansa ita. Ta sake gyada kai tana godewa Allah da tunda asuba aka gaya mata isowar saqon,kuma duka a yau zata iya yiwa akhnan amfani dasu,iyaka dai kawai ta barta subi jikinta na kwana uku kawai shikenan ta miqa masa matarsa. Yinin ranar ta sani za'a iya samun yaiwatar zirga zirga da jama'a. Saboda walimar da hussam ya shirya zaiyiwa haisam din. Nanay din tana jinsa yanata mita. "Karma kaje kayi abinda ba zai burgeshi ba.....shigar jubah zamuyi,kowa ya saka thobe kawai" Ya fada yana ya mutsa fuska,tana jinsa ya bada kalan shigan da za'a yi na jallabiyya,color kowa ya zabi favourite colour nasa. Breakfast kawai akhnan din tayi,zenebe da wata mata da ba zata iya tantance qabilarta ba,sukazo suka dauketa saboda gyaran jiki na qarshe da zasuyi mata,suka zagaya da ita baya inda nanay tasa aka kebance wani guri na musamman don suyi komai acan. *H A I S A M* Ya kammala shirinsa gaba daya na tafiya a yau din,wuni guda yana kai kawo bai zauna ba na hada sauran takardu da komai da zaya buqata,saidai ko sau daya bata bar tunaninsa ya huta ba. Baisan me yasa baya samun wayarta ba,saidai abinda bai sani ba nanay ta karba ta kashe. Can qasan ranta tanaso yayi missing akhnan dinne,tanaso yaji ya matsu da ita da gasken gaske,sannan kuma tana tsoron abinda ta gani a idanun akhnan din. Rauni da wata irin QAUNA data fara hange ta bata tsoro,kada ya hure mata kunne ya bata shirinsu na kwanakin data tsara. Zuwa yammaci aka soma gudanar da walimar. Cikin wani irin ba zata da bai zata ba saiga team dinsa dukkaninsu. Naseeb.....mutallab.....amjad......khadeem sai omar. Maleek kam yana can ya maqale,yace har yanzu honeymoon yakeci. Yayi mamakin ganinsu,saboda dukkaninsu zasuje bikin bude company a dubai nan da kwana biyar din daya rage,saidai kuma mamakinsa baiyi yawa can ba,don dukkaninsu suna dasawa da hussam. Baisan me yasa sukeyin hussam din ba,ko don zubin vibes dinsu yana zuwa daya dasu wani lokaci,saidai dukkaninsu a ranar kowa zai koma bakin aikinsa,tunda tafiya ce ta jirgi. Daga cikin gidan ma still wani walimar ne da Aanani da rumaisa suka shirya,harda noorah. Ita kanta nanay batasan sun shirya kayarsu ba. Daya daga cikin dakunan taro na gidan suma sukasa aka shirya musu shi da sauran qawayensu,dukkaninsu kuma shiga ce sukayi ta gargajiya,ta aninihin tufafin yaren oromo da suturarsu da yake zuwa kaloli biyu (Zan saka a status dina na watsapp in sha Allah,kusan tafiyar namu gani da jine😄). Ranar sai gidan ya zama hidima kawai akeyi,hakan ya yiwa nanay daidai,itama taga kawai gwara a kammala komai ta bashi matarsa kafin yakai ga fada mata gaba da gaba. Saidai nanay din batasan kalan tsiyan da yake qullawa ba. Da yammacin dab da faduwar rana kayan da suke nuna girmamawar ango zuwa ga amaryarsa a qabilar oromo suka iso. Koda ba'a gayawa kowa ba zakasan kayan mene tunda an riga an saba. Ya sameta a cikakkiyar mace da takai budurcinta. (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) (A kowanne yare.....a kowacce al'ada,a kowacce qasa.....a kowanne gari BUDURCI abune me muhimmanci....kada ki yarda.....karki kuskuren da zaki rasa baki a banza a wofi,ki tabbatar duk runtsi duk wuya duk gwagwarmaya kin kai naki dakin mijinki,mijin nan da yasan darajarki,yabi dukkan matakai ya biya sadakinki,wallahi ba wani abu.....ba wani gyara da za'a miki a rudeki ace budurcinki zai dawo,qarya ce wallahi wallahi tallahi,ko waye ya gaya miki ya yaudareki,hajiya kayan kamfani daban daban dana shago,ba wanda ya isa ya halicci wani abu da yayi daidai da wanda ubangiji ya halitta tun asali tun haihuwa,Allah ya bamu ikon kai zukatanmu nesa ameen summa ameen). Jikinta yana tururi da wani sample na ruwan wanka da turare da aka bata a daren tayi wanka dasu bayan an tashi walimar ta fito daga bandakin,saidai qarar shigowar saqo wayar da yanzu yanzu aka kawo mata ita ya sanyata dakatawa daga tsane jikinta da tayi ta dauki wayar tana dubawa. _"Wear something comfortable_ tomorrow morning _And don’t ask questions yet_ _Haisam_ Juya wayar ta dinga yi kawai ba tare data fahimci komai ba. Shigowar Aanani da murmushi tana ajiye mata sauran gifts din da suka kusan cike rabin dakin ya sanyata sauke wayar "Na gaji giifii.....ko na sanya su obsa su qarasa shigo dasu da safe?". Idanu waje kadan akhnan ta fidda. "Wai baki gama ba?" "Da ragowa" Ta amsa mata tana daidaita zaman wani kwali. "Ki huta sistern captain obbo.....sai goben" Dariya sosai Anaani tayi. "Da zaijiki kuwa zaice....wannan me kunnen qashin?,noorah ce tawa" Da murmushi ta bita da kallo harta fice,sai taji inama itace su,gasu cikin rayuwar da suka tashi tsakanin qannensu da yayyensu. Akwai wani irin so qauna da respect da suke bawa junansu,musamman haisam din. Ta karanci wani irin so kowa cikin 'yan uwanshi yake masa,saita ture komai ta soma shafa mai tana jiran birra ta qaraso ta bata rigan bacci. Tabi tarin kyaututtukan da kallo,qawayensu da abokan hussam ne kawai suka hada mata uban kaya haka. Mamaki takeyi na yadda suke da kyakkyawar mu'amala da mutane da yawa. Kaman girma da qarfin iko na masarautarsu bai daukesu ya d'ad'asu da qasa ba. Suna wani rayuwa simple,izzar ke magana da kanta basu ke qoqarin gwada ikonsu ko nunata ba. Sanda dare ya fara nisa sai bacci ya gagareta. Daren jiya take tunawa,kowanne moment daya shude,kowanne second minti da awa da suka qarar ita dashi,sai ta kuma samun kanta da jin kamar motsinsa,kamar takunsa da tafiyarsa,ta runtse idanunta sannan ta sake budesu a hankali,bashi ba alamunsa. Duka baccin sai taji yana neman qaurace mata,ta samu kanta da tuhumarsa.....me yasa baizo kaman jiya ba?,sai kuma dariya ta subuce mata sanda zuciyarta kece mata. "Kece bakiso....kin manta?,amma yanzun kike nemansa?" Murmushi ta saki tana cusa kanta cikin pillow din da har yanzu bar mata qamshinsa. ★Farar cotton din riga ce a jikinta me zuwa hade da hijab saqar qasar Malaysia,wadda aka yita musamman saboda gudanar da ibadar sallah. Kallon wayarta ta sakeyi a karo na biyu da saqonsa ya shigo mata,tsoro da mamaki cakude akan fuskarta,tuni ne dai yake sake mata. "Minti goma sun shude.....mintuna biyar suka rage idan baki fito ba.....zan shigo har ciki,zan kuma daukeki ko a gaban waye" A jikinta takejin zai iya,a jikinta takejin zai aikata,saita sauke wayar a hankali zuciyarta tana wani bugawa. *zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 08187255862 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 08187255862 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 90* _______________________ https://chat.whatsapp.com/IZGMwJXP8Oa5qUc4sDSKZv?s=cl&p=a&mlu=3 *_YI JOINING DON SAMUN DAMAN KOYAR ABUBUWA KAMAN HAKA_* Abaya Stone laffaya Glitter laffaya Stone veils Glitter veils Bead work Paint work 08036027448 *_Karki bari wannan sassauqar damar ta wuceki_* ____________________________ Qarfe shida ne na safe,meye ya faru da zaice lallai saita take dokar nanay ta fito da safen can bayan sassan nanay?. Ya bari kowa ya tashi,ido na ganin ido ya shigo ganta mana?. Kafin ta sauke wannan tunanin kiransa ya shigo kai tsaye. "Gan.....ganinan" Ta fadi muryarta tana rawa kadan. Saita zame wayar daga kunnenta tana ajiyeta. Tsoro take kada ya shigo kaman yadda ya fada,ya taho dakin kansa tsaye,taje suyi kacibus da nanay,to tace mata me?,ta kare kanta da wacce hujja?. Slippers masu tashi ta saka bayan ta daure igiyar hijabinta a bayan kanta,wanda hakan ya bawa tudun gashinta dake boye a hijab din nunawa. Kamar wata barauniya haka take takawa,sannu a hankali tana bude parlours da dakunan zaman baqi tana bin direction din daya gaya mata. Har ta gama shiga da fita zuwa hanyar da zata kaita bayan sassan ba wanda ta gamu dashi,sai a qofar qarshe rumaisa ta tura tana shigowa hannunta dauke da wani file. Baya taja da sauri tana bawa akhnan hanya fuskarta da murmushin girmamawa tadan rusuna,duk da ta girme mata kadan. "Barka da safiya matar captain".murmushi akhnan ta qirqiro,don har ga Allah adan rude take. "Barka kade likitarmu.....mun tashi lpy?" "Lafiya alhamdulillah,ya gajiya,ina fatan bamu gajiyar dake ba" "Alhamdulillah likita" "To ma sha Allah,bari na qarasa ciki,saikin dawo" Rumaisa ta fadi tana yin gaba. Da dan mamaki akhnan tadan bita da kallo,basu da damuwa kuma basu da matsala,sanya idanu ko bin qwaqwafi. Wata rayuwa suke simple,basu matsawa rayuwar kowa ba. Inda watace,koda bada wata manufa ba saita tambayeta ina zata je?,amma ita tayi gaba abinta tana sabgar gabanta kawai. Maida qofar tayi tana ficewa tare da qoqarin bin hanyar daidai. Komai fari ne a jikinsa,tun daga kan jallabiyyar jikinsa har xuwa thobe din dake matsayin kamar after dress daya dora saman jallabiyyar. Hakanan takalmin qafarsa.....da amam din daya dora(rawani),wanda ya masa wani irin nad'i dake nuna zallar qwarewa wajen sarrafa daurin rawani saman kai. Ya fita fes.......sak matashin yariman malamin nan da duniya keyi dashi. Ilimi.....kyau sarauta da dukiya gaba daya. Qamshinsa kawai ke kai kawo a gurin da wani tattausan yanayi daya saje da safiyar ranar,safiyar da ba wata wadatacciyar alamun samun rana a wunin gaba daya,saboda yadda hadari ke lullube da ko ina. Idanunsa ya zube fes a kanta,idanun nasa suna lumshe kansu suna kuma budewa. Farar fata cikin fararen kaya,wani mugun kyau tayi masa,tamkar sabon fure daya fita a ranar,aka samu arashi kuma wadataccen ruwan sama ya sauka a ranar. Wani irin abu yakeji yana fusgarsa zuwa gareta......kyawawan blue eyes din nan nata da suke juyawa a hankali,da alama tanason hango inda yake tsaye. _ki taimakeni karki fadi.....idan kika fadi har cikin zuciyata ciwon zai kasance......ki kalli gabanki_ Saqon daya shigo wayarta kenan,idanunta ta daga a hankali bayan ta gama karanta saqon tana miqar da kallonta zuwa gabanta. Yana jingine da wata farar mota qwaya daya,kansa da idanunsa dukka suna kan wayarsa. Ta lumshe idonta tana hadiye wani abu a hankali. "Ya hadu" Ta fada can qasan maqoshinta tana motsa labbanta a hankali. Karo na farko da idanunta ya taba sauka akan wani d'a namiji taji ya wuce da dukka numfashinta da nutsuwarta. HAISAM.....wani namiji da yasha wucewa da numfashinta.....tunaninta......nutsuwarta dama komai nata. HAISAM d'a namiji a duniya na farko daya taba mallakar tunaninta da zuciyarta,daga qarshe ma ya mallaki gangar jikinta gaba daya......itakam ta yaya zata iya rayuwa ba tare dashi ba?. A iya jiya kadai ta fadawa kanta wannan maganar har batasan adadi ba. Rashinsa a kusa da ita kawai ya sanya baccinta ya zama wani iri......ina ga ranar da zata bude idanu ta tsinci babu shi?. Wannan JAN AJIN nasa......da wannan basarwar tasa yabar kansa saman wayarsa Kamar ba shine ya hangota yayi directing nata zuwa inda yake tsaye ba. Sai zuciyarta ta soma motsawa da wannan kalar kishin nasa. Kishinta a yau akan wayarsa yake,karo na farko data fara jin tana kishin wayarsa sosai kamar d'an adam. Yasan ta taho....me yasa bazai bar kallon wayarsa ya kalleta ba?. Tambabayar data qaraso da ita gabansa kenan,saidai tabar tazarar taku kusan biyar tsakaninsu. "Ina kwana?" Ta furta a hankali daya daga cikin lectures na nanay suna mata tasiri ciki tunaninta. Dukka juriyarsa ce ta qare,ya cire kansa daga wayar ya zube mata narkakkun idanun nan,wadanda da qyar suka samu bacci a daren jiya saboda matsananciyar kewarta. Baije gareta ba,saboda yanaso ya yiwa kansa control......yanaso ya barta ta huta,yanaso ta dawo nutsuwarta ta rage tsoron daya yake gani nasa a idanunta. Kamar wanda abinda ya kawoshi kenan kawai shine kallonta,ya tsareta da lumsassun idanunsa wanda idan kana dan nesa kadan dashi zaka dauka a rufe suke ruf,saboda yadda sukayi laushi sosai,sannan eyelashes dinsa suka sake taimakawa wajen yiwa idanun nasa rumfa. Ji yayi kowacce kalma ta maqale a maqoshinsa,bazai iya amsa mata ba,sai kawai ya matsa daga jikin motar ya bude murfin ya juya ya mata alama da idanu na ta shiga. Motar ta kalla sannan ta kalleshi da tambaya fal idanunta,idonsa ya lumshe mata yana girgiza mata kai alamun bayason tace komai,saita hadiyi wani yawu a hankali ta tattara qwarin gwiwarta tunaninta yanason canko mata abinda yake shirin yi "Wannan fa kamar laifi ne" Ta fada blue eyes dinta suna tara qyallin hawayen tsoro. Ya gani.....yaga komai dake idanunta. Ya karanci kamar sun hada baki ita da nanay ne sunason wahalar dashi,sai ya soma takawa majestically yana nufarta,bai kuma tsaya ba,sai daya cike duk wata tazara dake tsakaninsu. Qugunta ya riqe sosai ta cikin tattausan tafin hannunsa yana sake jawota gabansa sosai Kansa yake qoqarin saukewa saitin wuyanta sanda yake bata amsa da wata kasalalliyar murya "Noooo....." Ya fada yana sauke mata muryar da nauyi cikin kunnenta. "It's called rescuing my wife" Ya fada yana daukarta cak yana rabata da qasa tamkar ya samu 'yar tsana. Ta tsorata da hakan,saboda abinda bata zata bane,suata qanqameshi sosai tana riqe wuyansa. Blue eyes dinta a waje sosai,wannan sassanyan qamshin nasa yana tururuwar shige mata hanci. "Shi bayajin kunya?,baya tsoro kowa ya gansu?,a haka?,a tsakiyar masarautar?". "Nanay zata...." Ta fadi sanda ya bude motar yasa qafarsa yana qara bude murfin motar sosai ya kuma sakata cikin motar kamar qaramar yarinya,saidai yadda ya zube mata narkakkun idanun nan nasa ya sanya ta kasa qarasawa. "She'll forgive us eventually....." Ya amsa mata da yaren French da a yau taji ya sake taushi cikin harshensa. Sukunyawa yayi ya bata wani soft kiss,ta lumshe idanunta tana jin sanyin labbansa akan goshinta. Ta kasa bude idanun tayi shuru tana sauraren yadda zuciyarta ke bugawa cikin nutsuwa,har zuwa sanda ya rufe murfin motar,taji shuru nadan sakanni sannan ta jishi ya shigo gefanta. "Mu tafi" Ya fada da muryar umarni cikin yaren oromo. "Ina zai kaimu"? Ta tambayi kanta a nutse sanda take bude idanunta lokacin da taji wannan tattausan tafin hannun nasa cikin nata. Ya sauke wani abu a kowanne sashe na jikinta,wani irin dumi da tafin hannunsa ke dashi.....wani irin laushi da tasha tambayar kanta. "Dukka maza haka tafin hannunsu yake?,ko nashi ne haka?" Kansa taji ya kwantar a hankali saman kafadarta,da wani irin yanayi na shagwaba da narkewa. "Good morning my princess......." Ya fada yana matse tafin hannun nata a cikin nasa ba tare daya qarasa fadin abinda yaso ya fada din ba,yana jin wani yanayi yana mamayar jikinsa a hankali. "......Good morning to the woman currently occupying most of my thoughts" Ya sake fada da wani irin taushi yana saka hannunsa ta baya ya zagaye qugunta. "Morning" Ta fada tana jin yadda harshenta da muryarta suke sarqewa gaba daya. Wani irin kusanci yake bata......wani irin kusanci yake kawowa tsakaninsu da takejin ba zata jure ba. Batason ta sake wani abu da zata bada kanta irin wanda tayi daren shekaran jiya. "Ina zamuje?banaso nayi nisa" Ta tambayeshi kai tsaye tana jin fargaba kadan. (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) Murmushi ya sake kawai,sai ya zame ya maida kansa saman cinyarta,ya kwanta rigingine yadda zai samu damar kallon kyakkyawar fuskarta data fito da wata irin kamala ta tsakiyar hijabin,wanda daga qeya acucin da tayi da tudun gashinta ya fito sosai. Hannunsa ya miqa a hankali ya shafi gefan fuskarta data masa kyau sosai,kaman dazun idanunsa suna lumshewa sannan su bude da kansu. Wani irin murmushi.......classy murmushi da bata taba ganinsa saman fuskarsa bane yake fita akan fuskartasa a yanzu. "Ina zamuje?" Ta sake maimaitawa tana qoqarin riqe hannunta da a yanzu ya sanya yatsarsa yana zagaya siraran labbanta. "Wata duniya......" Sai ya dakata kamar me jiran wani abu. "......inda daga ni saike" "Hh.....hais" Saita gaza qarasawa ganin yadda ya zubawa labbanta idanu. Ta tuna....sunansa duk sanda zata furta kamar yana kunna wani emotions ne cikin kansa,saita yanke kiran sunan. Da wanne suna zata kirashi ne?,wanda bazai tayar da wata fitina ba?. Murmushi ya kuma kasheta dashi,wannan soft dangerous smile din nasa kafin ya sake motsa labbansa. "Zan kaiki wajen da hayaniyar duniya ba zata samemu ba......" Shuru "Wajen da babu kowa da zai rabamin ke" Shuru "Wajen da ba wanda zai sake daukemin ke" Shuru. "Khadeejaaah" Ya kira sunanta da wannan unique accent din da daga bakinsa kawai take jinsa. "Na gaji da sharing attention dinki da kowa" Ya qarasa fada yana ciro tarin ma'anoni daga qwayar idanun nan nata dake masa haske koda kuwa cikin duhu ne. "Me zamuyi a duniyar nan ko?" Ya fada yana dage mata dukka girarsa biyun sama. Idanunta ta kawar tana jin kansa sosai har cikin naman cinyarta,tana jin sauti sa muryarsa kallonsa da idanunsa dukka suna sake narkar mata da zuciya lokaci guda a tare. "We'll breathe" Ya dakata a tausashe har yanzu hannunsa yana shafa fatar fuskarta da ya sakeji ta masa wani irin fitinannen laushi. "We'll rest" Ya sake dakatawa a kasalance "And may be......" Ya sake tsayawa "......finally learn each other properly" Idanunta ta lumshe a hankali. Yadda yake maganan a rarrabe kanshi wani abu yake saukar mata. Tamkar dai yana zaben kalmomin da yakeso yayi maganan ne dasu,ko yana qoqarin kiyaye abinda tafiso cikin dukka jimlolinsa. Hannu ya miqa a hankali yana shafa kwantaccen gashin dake gefan kunnenta,wanda a baya yake kira da sajen mata. Daya daga cikin wasu abubuwa da yakeso matuqa a fuskar diya mace. "Inaso wajen da idan na kalleki....." Sai ya sake dakatawa,muryarsa kuma ta sakeyin qasa fiye da dazu kamar me tsoron wani zai iya jinsa. ".......bazan riqa jin lokaci yana gudu daga gareni ba" "Kana magana kamar a mafarki?" Ta fadi ba tare data shiryawa fadin hakan ba,sai don abinda yake kai kawo kenan a ranta. Wanne guri ne wannan?,wanne abu ya shirya mata?. "No...." Ya fada da murmushi ne dan sauti Yana laluben qwayar idanunta yanason ya riqeta sosai cikin tasa,saboda yana son ta dauki duk abinda zaice mata seriously. "I'm talking like a man who finally found peace......" Ya sake sauke wani numfashin,ya juya ya koma rub da ciki yana qanqame cinyoyinta sosai. ".......and is terrified of to losing it". Wani irin shuru ya ratsa tsakaninsu,wani irin shuru da bugun zuciya kawai ya bari a tsakaninsu. Bayan kowanne second sake kasheta yakeyi da kalamansa......da ayyukansa dama shigarsa gaba daya. Kalamansa zata iya rantsuwa da Allah bata taba jin masu zaqi irinsu ba.....bata taba jin zababbun kalamai irin nasa ba,wai dama haka malaman suke?,ko shine na daban?,ko shine ya fita daban a cikinsu da cikin maza gaba daya?. *zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 08187255862 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 08187255862 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 91* _______________________ DEA’S MODEST ARTISTRY ✨ Aminataccen wajen samun ✔️ Abaya masu kyau ✔️ Lifaya & Veils masu tsari ✔️ Handmade paint work ✔️ Shadda designs ✔️ Elegant modest wears ✔️ Accessories masu kyau da inganci Muna kawo muku kaya masu kyau, tsafta da araha domin kowane irin event 💫 Ko na daily wear, outing, wedding ko special occasions — DEA’S MODEST ARTISTRY na tare da ke 🖤 📍Quality first 📍Affordable prices 📍Neat finishing 📍Classy & Modest styles Ki kasance cikin kyau da nutsuwa ba tare da tsada ba ✨ https://chat.whatsapp.com/IZGMwJXP8Oa5qUc4sDSKZv?s=cl&p=a&mlu=3 _________________________ Hannunsa ya miqa mata a hankali sanda yaji alamun motar ta tsaya. Ba don baya da ikon kamosu ba "Akhnan....." Ya kirata softly,yana kan cinyarta,har yanzu a rub da ciki,idanunsa kuma a kulle kaman bai shirya su sauka a motar ba. "......come with me please,na miki alqawarin baki duk kalan space din da kikeso......ba takura.....ba matsantawa.....just ni dake kawai,mu raini soyayyarmu....." Ya qarasa fada yana juyowa rigingine hadi da bude qwayar idanunsa dukka a kanta. Batasan me yajata ba,batasan yaushe ba. Ita dai ta miqa masa hannunta a hankali,ya riqe cikin nasa da murmushi. "Bazan saki kiyi regretting ba har abada.....but.....kafin na sauke qafafuna qasa,kice kina sona.....ko sau daya ne.....don Allah" Ya fada yana langabe kai.....ya fada da kalar wannan sakalcin da taga yana yiwa nanay. Wata kunya ce ta dabibayeta,ta maida idanunta ta kulle a hankali. Ta yaya zata iya...... "Pleeeeeeeeaaaaaaseeeeeeeeeeee....." "I love you" Ta fada da sauri labbanta suna rawa saboda yadda ya gigitata da sautin da ya yiwa sound din wani mugun ja. Idanunta kawai ta kalmashe sanda suke takawa hannunta cikin nasa. Wani takun girma,royal walking suke dake bayyana iko ba tare da hayaniya ko qaqarin nuna kai ba. Komai da kowa yasan girmansa ba tare da yace komai ko yayi wani motsi ba. Dukkan ma’aikatan private terminal ɗin, manya da qanana, suna sunkuyar da kai cikin girmamawa yayin da suke wucewa. Kyakkyawan private jet din da suke tunkara,idanunta cike da tarin tambayayoyin data gaza hadiyesu sanda suke step na qarshe na jirgin. "Ina zamuje?" Ta tambaya tana langabe kanta a wannan karon. Ta gaji da tarin mamakin da yake bata,ta fahimci shi din wani allo ne da har yanzu bata kammala karantarsa ba. "Dubai" Ya amsa mata a taqaice yana gyara mata gefan hijabinta cikin kulawa. "Dubai?" Ta fada da mamaki fal muryarta idanunta suna dan fita waje kadan. "Eh...." Ya amsa yana satar kallon reaction dinta. "Ina neman na abinci ne a wani kamfani,sai suka gayyaceni wani taro da zasuyi" Shuru tayi bawai don ta gamsu da hujjar daya bata ba dari bisa dari. Saidai tayi shurun saboda tasan ba zata fahimci komai ba sai idan shi yaso ta fahimta din. Abu daya kawa daya sanyata mutsu mutsu,ta dinga jin kamar ta roqeshi.amma ta kasa,kasancewar bata saba neman alfarma akan kowa game da komai ba. "Me yake faruwa?" Ya yambayeta tana dubanta da lumsassun idanunsa. "Akwai wani bikin bude company branch na favourite perfume dina.....a dubai ne.....date din saura kwana biyar.......don Allah.....zaka barni naje?" Ta fada da wani salo da yanayin daya qarasa karyashi gaba daya. "Ya salaammm" Ya fada yana duban qwayar idanunta. Ashe ta iya magiya?,ashe ta iya karyar dakai har haka?,wanne irin so takewa kamfanin da turaren haka. "Sun iya turare......best perfume brand ever" Ta sake fadi duk a qoqarinta nason amintar dashi. Yadda take magana yana burgeshi,yadda idanunta ke budewa sosai,take sakewa tana magana dashi tafiya yakeyi dashi. Bayason wannan yanayin ya yanke da sauri haka,don haka bai amsa mata ba,sai yaci gaba da kallonta kawai. "Don Allah.....zan aike musu email na neman invitation din. Nasan zasu bani indai sukaji daga agadez ne. Ko ban samu shiga ba,zan tsaya na jira ganin founder na company din". " Zakije....zaki shiga.....in sha Allah". "Na gode" Ta fada da wani irin murna har tana rungumarsa bata lura ba. Sai kuma tayi yunqurin janyewa da sauri,saidai ya rigata da zafin namansa,ya jawota zuwa cikin jikinsa yana cewa. "Good girl,wannan shine lada na ai,ya zakimin rowa?" Murmushi ya qwace mata a kunyace,ta saka fuskarta tsakanin qirjinsa,ta lumshe idanunta tana jin sassanyan qamshin dake fita daga tsakiyar gurin "Ya Allah......Wani irin qamshi ne wannan?..…Too elegant for one man.” saita sauke numfashin a hankali tana zame jikinta,ya saketa a nutse ba tare daya qalubalanci hakan ba. *_DUBAI INTERNATIONAL AIRPORT_* A hankali private jet dinsu ya sauka akan runaway cikin tsari,ba'a babban airport na gama garin jama'a ba,aah...cikin private Royal terminal . Guri ne da luxury jets kawai ke sauka ta nan,gwamnoni....sarakuna....da kuma manyan billionaire's. A hankali ya sauke idanunta ta cikin window din tana kallon qasa,jerin motoci ne baqaqe dake sheqi da daukan idanu a jere cikin tsari suna jira. Luxury SUVs. Rolls-Royce Phantom. Sai security convoy.. Da idanun ba kuma tare data sauka ba ta fahimci yadda komai na gurin ke dauke da nutsuwa da wani irin tsari ba tare da hayaniya ba. Irin tsarin da zai gaya maka akwai mutum me daraja da girma da ake jiran isowarsa a gurin. Ya miqe tsaye daga kujerarsa cikin nutsuwa. Cuff din hannunsa ya gyara,sannan ya dauki agogonsa yana qoqarin maidawa tsintsiyar hannunsa. A sace ta kalleshi,komai nasa yana nuna old money discipline,ba hayaniya.....ba nuna kai,saidai a jikinka kana iya jin presence nasa saboda kwarjinin da Allah yayi masa. Komai nasa cikin nutsuwa da sanin girma kai,yana komai cikin yanayin da zai gaya maka nutsatsen mutum ne shi da bai taba gaggawa ba a komai. "Ready?" Taji ya furta a hankali,abinda ya sanyata saurin janye idanunta daga kanshi kenan ta sake maidawa ga window din zuciyarta tana wani irin bugawa. Kada dai ace yaga yadda take qare masa kallo?. Ya yanke mata tunaninta sanda yake sunkuyowa inda take,ya sanya hannuwansa gaba daya yana dagata tsaye,sassanyar iskar hancinsa tana dukan fuskarta wadda ke cakude da turarensa dan amana. "I'm your halal.....dukkanina khadeejah....halal dinki ne,ki kalleni as much as you can.....ba laifi...." Sai ya dakata kaman yadda maganansa yake a tsare. Yatsansa ya daga yana nuna saitin qirjinta dashi. "Kibar wannan mallakin tawa ta huta....ki daina razanata haka kina sanyata tana gudun wuce kima". Tsit tayi tana kasa hada idanu dashi,gaba daya ya qarasa qona mata ruwan kai,ta fahimci al'adarsa ce.....yana da basarwa,ya gani yayi kaman bai gani ba.....yaji yayi kaman baiji ba,haka tayita gasa masa magana akan French language,amma yanzu ta zama tamake 'yar koyo a gabansa,har ba komai takeson tayi magana akai da yaren ba. "Ready again?" Ya sake fada yana tsaronta kayarsa da qwayar idanunnan nasa. (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) Kalma daya.....amma daya fadeta sai taji kamar umarni ne da zuciyarta ta riga ta yarda dashi kafin karan kanta. Hannunsa ya sake miqa mata,a yanzun ma ba wani haufi ta saka nata a ciki. Matseshi yayi softly yana duban blue eyes dinta. Bada qarfi ba,amma kuma kaman yanason ya tabbatar mata da ownership dinsa ce ita me cike da kariya daga garesa. Daya bayan daya suke takawa har zuwa bakin jet din. Royal walking,wata irin nutsuwa me bayyana girman da basai an fada ba. Daddadar iskar dubai ta soma sauka saman fuskarta,warm elegant dauke da wani qamshin alfarma. Idanunta ya sauka akan mutanen dake tsaye suna jiran saukowarsa. Hotel representatives.....business officials.....security chiefs da personal staff's wadanda kowanne shigarsa ta bayyana matsayinsa. Bayansa kadan ya sanyata,kamar wanda ke boyonta kada a kalle masa ita,cikin madaidaicin takunsa ya soma sauka,me cike da ginshira da qasaita. Tana biye dashi,still hannunsa bai zame daga nata ba. Haka kawai wannan karon tsaiwar tarbar tasa yaji ta takureshi. Gani yake kaman kowa ita yake kalla,kaman ita daya tayi saura halittar diya mace a duniya. Musamman abayar dake jikinta yanzu,royal silk ne me asalin tsada da kauri da kuma daukar idanu. Shi da kansa data kammala shiryawa ta fito sai daya jima zaune,ya sanyata tana tsaye a gabansa yana qare mata kallo,ya fusgi kalmar "Ma sha Allah" Da wani sanyin jiki da kasala da kallonta kawai yake saukar masa dashi. A hankali ta lura da wata kalar girmamawa daga dukkan wanda yake gurin. Duk wanda haisam ya isa gabansa sai taga ya sunkuyar da kansa kadan kafin ya bawa haisam hannunsa suyi musabaha. Cikin ladabi dukkansu suke kiransa. "Welcome back mr aba jifar" Sunan daya tsayawa akhnan sosai a ranta. Ba wai don yau ta fara jinsa ba.....aah,sai don yadda take ganin dacewar sunan dame shi. "Thank you" Yake amsa musu dashi,saidai saman fuskarsa akwai murmushin daya rage miskilancin saman fuskarsa. Kaman yasan ta shiga wani tunani na daban,ya matsa yatsunta a hankali kamar yana tuna mata cewa yana tare da ita ne. "Don't look so startled.....they're only being polite" Ya fada calmly. "Only being polite?" Ta maimaita kalmar a cikin kanta. Wasa yakeso ya mata da hankali kenan kamar yadda ya saba?. Ta sake maimaita kalmar.....alhali mutanen suna kallonsa da irin girmamawar da akewa sarakuna. Yarima ne shi ta sani....ba wani sauran abinda zai boye mata.....sai sauran abinda bata sani ba. Wani daga cikin mutanen ne ya matso,hannunsa dauke da tablet "The palace district has been informed of your arrival sir" Kadan taji numfashinta ya tsaya "Palace district?" Ta sake maimaitawa qasan zuciyarta. "And everything has been prepared..." Ya qarasa maganan yana miqa masa tablet din. "Good" Haisam yace kawai yana riqe tablet din cikin hannunsa,mutumin ya gyada kai kamar wanda aka bawa lambar yabo yana matsawa a gurin. Sake riqeta yayi a hankali tana daga bayanshi suna takawa. Idanunta na cikin airport din zuwa motocin da suke dosa,amma kunnuwanta suna jiye mata sautin haisam. Sautinsa ne.....saidai a yau din da wani yare da wani harshe da bata taba ji yayi magana dashi ba. Harshen larabci....mafificin harshen da a duniya shine yare na daya da take matuqar son taga ta iya. Yana mata wani irin dadi.......tana jin wata nutsuwa a duk sanda ake yaren,koda kuwa bata fahimtar komai a cikinsa. Duk da tarin mutanen dake neman yabawarsu wajen girmamashi......amma hakan bai hanashi barinsu ba,ya matsa a nutse ya bude mata qofar Royce rolls din yana duban idanunta da girmamawa. Takawa tayi a nutse zuwa cikin motar,saidai idanunta a kansa. Kowacce rana sake bata mamaki yake,kowacce rana bayyana mata kanshi yakeyi ba tare da yayi magana da bakinsa ba. Dangerous calm smile dinsa ya sakar mata,sannan ya zagaya a nutse daya daga cikin guards dinsa suna bude masa tasa qofar. "Wane irin mutum ne wannan?,And how much of him have I yet to discover?" Ta yiwa kanta tambayar sanda convoy din motocin ke motsawa a hankali suna barin harabar airport din. Bata sake sanin cewa ta shiga duniyar mutumin da take tunanin kawai ta sanshi bane.....bata sake sanin a yanzun bane zata fara sanin.....zata kuma fara ganinsa da gaske ba sai sanda suka isa harabar hotel din. "Ya salam ya Allah" Ta fada can qasan maqoshinta lokacin da motocinsu ke qoqarin sanya kansu farfajiyar hotel din. *_Turqashi!!!.....haisam ne akhnan......akwai saura.....baki gama shan mamakinsa.....ki adana mamakin nan kada ya qare.....ba akhnan ba.....ko ni da naga hotel din an gama tashin kaina 🧐🧐,mu hade gobe in sha Allah with scene view na hotel din in sha Allah kaman yadda muka saba_* *_INA FATA BAKU MANTA BA....WANNAN WEEK DIN NA DABANNE NACE KO IN SHA ALLAH_* *HUGUMANKU CE*🙌🏽🙌🏽🙌🏽 *zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 08187255862 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 08187255862 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 92* __________________________ https://chat.whatsapp.com/BkfPzSEDhnsIwyCD8LNGkm?s=cl&p=a&mlu=0 *IDAN KINSAN BA ORDER DIN KAYA ZAKI DINGA SAKAWA BA* *IDAN KINSAN BA BUSINESS KIKE DA NIYYAN YI NA KAWO KAYA DAGA CHINA BA KARKI SHIGA* *_DON ALLAH KARKI BATAWA KANKI LOKACI_* *_Assalamu alaikum my loyal people_* *_Barkanmu da wannan lokaci,kuma barkanmu da warhaka_* *_akwai da dama cikin mata wadanda suke sha'awar yin order kaya daga CHINA zuwa NIGERIA,NIJER,CAMERON,CHAD da GHANA_* *_Amma rashin samun amintaccen company....ko hannun wanda zasu dinga siyan kaya ta hannunsu cikin aminci ya hanasu_* *_To a yau addu'ar da yawa daga cikinku ta amsu,don nayo muku tsarabar kamfanin da zakuyi siyayya ta hannunsu su kuma dora muku kayanku har qasarku cikin aminci ba tare da fargaba ko d'ar d'ar ba_* *_kunsan komai nawa TASTED AND TRUSTED ne,to wannan kamfanin idan akwai abinda yafi TASTED AND TRUSTED ma shine_* *_Baki da fargaba kota sisin kwabo,ni SAFIYYA HUGUMA na tabbatar da hakan_* *_Zaki iya kasancewa dasu group nasu,inda a nan zaki hadu da agent dinsu da CEO nasu gaba daya ta wannan link din,zaki samu bayanansu da komai da ya shafi mu'amala dasu_* *INA ME BAKU TABBACIN AMINCI DA INGANCI DA SAUQIN MU'AMALA DASU DA IZININ ALLAH,BAN TALLATA MUKU SU BA SAI DANA GWADA* *Allah ya dafa mana,yasa mana albarka a nemanmu,ya albarkaci halal dinmu ameen summa amee* _________________________ *_ATLANTISTHEROYAL_* .......Hotel mafi tsada a dukka hotels na duniya. Hotel din da bata taba kawowa a kanta zata shigeshi ba. Dream hotel dinta.....ba ita kadai ba,hatta da aisa shehnaz dama duk wanda ta sani suna tafiye tafiyen yawon bude idanu. Yanzun kam kai tsaye take kallon haisam. Tana ganin ta gama saninsa,tunda tasan cewa shi din yarima ne,dan sarkin jimma. Tana tunanin ta gama saninsa tunda tasan family dinsa......amma saidai a yanzun ta fara qaryata wannan. Bai kula da kallon da take masa bane.....ko basarwar daya saba ne cikin jininsa oho,bai waiwaya ba har zuwa sanda motar ta gsayata qawatacce kuma tsararren gurin adana motoci,ya sanya hannunsa ya bude side dinsa. Ta glass din tana iya kallon yadda yake sallama da mutananen da suka masa rakiya. Da wannan yanayin da zai gaya maka tabbas an haifeshi ne a cikin IKO.....ba kuma shike neman ikon da girma ba,sune suke bibiyarsa. Takunsa a nutse.....wannan royal walking din ya qaraso gaban motar,ya sanya hannu ya bude mata hana dubanta a tausashe. "Bismillah.....my princess" Idanunta ta lumshe a kansu,sannan ta budesu lokaci daya. "Bazan iya saukowa ba......alhalin har yanzu ban gama sanin waye kai ba" Idanu ya zaro gaba daya mamaki yana bayyana saman fuskarsa,kafin kuma a hankali ya maye gurbin mamakin da murmushi. Matsowa yayi gaba kadan zai riqe hannunta amma ta janye "Is okay....." Ya fadi shima yana maida hannunsa ya hade tafukan hannayen nasa yana murzasu guri daya. "Kiyi haquri....." "Nayi.....kuma zanyi,bazan matsa maka ka gayamin komai ba,har sai sanda ka shirya......amma zuwa yanzu.....duk abinda na gani na tambayeka lallai zaka bani amsarsa.....wannan shine sharadin shigata ciki" Ta fada tana dan bin ginin hotel din da kallo. Shuru ya danyi,kamar yana nazarin wani abu,sai kuma a hankali ya gyada kansa yana lanqwasar da kansa cikin yanayi na girmamawa. "Accepted your royal highness" Ya furta yana saka tafin hannunsa a qirjinsa. Cikin jikinsa ya riqeta sosai,yana jin kamar zata bace masa ne. Idanunta a hankali suke qarewa hotel din kallo,zuwanta na farko kenan saidai gani a hoto da videos. Wasu irin palm trees masu haske da qyalli da suka qawata shi a jere gefe da gefensa. A zahirinsa yafi mata kyau,yafi kama da modern palace. Qofar main entrance na hotel din,doormen din suka matsa cikin girmamawa,matsawar tasu ya bashi daman ganin wadanda ke tsaye suna jiransa. Security da managers ne na hotel din,wani irin fountain light. Crystal reflection tako ina,ga wani irin fresh oud scents dake yawo a cikin iskar gurin. "Welcome back sir" Managers din ke fada cikin girmamawa. "Welcome back" Ta sake maimaitawa. Hakan na nufin ya saba.....ya riga ya saba da zama kenan a gurin?.. (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) Larabcinsa dasu yaci gaba da shiga kanta,ta sake lumshe idanunta tana jin tarin tambayoyi a kansa suna cika mata kwanya. Yanayin accent dinsa ya fita daban da nasu,ta kasa tantance a cikinsu waye yaren yafi zama da dadi akan harshensa?. Zata iya cewa SHI duk da hakan zai zama kamar wani son kai ne tayi,saidai kam zata zabeshi ta sake zabinsa saboda. Husky voice dinsa da take zama very calm da wani irin soft tone yadda take fita yasha banban da nasu,ta saba jin hakan,muryarsa daban....da wani irin banbanci da muryar kowanne d'a namiji a duniya. "Your penthouse was ready" Muryar daya daga cikin staff din ta fada. Godiya ya masa kaman yadda ta lura dabi'arsa ce ga duk wanda ya masa hidima,sannan kowa ya qyaleshi da ma'aikatan hotel din biyu da security din data kasa ganewa nasa ne tun asali ko a nan yayi hiring nasu?. Penthouse kawai ke yawo cikin kanta,idanunta kuma suna son gane mata zahirin abinda kunnuwanta sukaji mata. Private elevator suka shiga,iya shi da ita kadai,sauran suka shiga wata don su tarar dasu a building din da zasu sauka. Ya matsa ya bawa elevator din number building din,tayi tsaye a bayansa tana kallon yadda yake tsaye. Cikin nutsuwa da kamewa,da wani kalan hali da dabi'ar da bazaka taba zaton ya taka irin wannan matsayin ba a rayuwarsa. *_Mr aba jifar hallway_* Abinda ta gani kenan a rubuce jikin wani arrow na silver bayan fitarsu daga elevator din. Mamaki yana sake kasheta,private floor?,dama akwai private floor a hotel?. Residence guda take gani a rubuce,bawai suit da suka saba sauka ba?. "Mallakinsa ne kenan wannan ginin?" Tambayar da taji ta mata girma akai. A hotel irin wannan.....wanda kwana daya tal a cikinsa girma ne.....nasara ce......daraja ce da alfarma,amma a ciki har ace wani dan adam ya mallaki sashe guda nasa na qashin kansa.. "Who is muhammad haisam aba jifar?" Tabbas akwai wani.mutum still a boye a bayan wannan sunan.....a bayan wannan fuskar.....a bayan duka abinda ta sani. Ba basarake kawai malami ba.....tana hangen zai iya zama wani billionaire ne?...... Tambayar tayi tsawa cikin kanta ta kuma sake daga kai still tana kallonsa ta gefan fuskarsa. Ta sake daga idanunta,a entrance na private hallway din akwai engraved silver plate dake dauke da sunan PRINCE HAISAM ABA JIFAR RESIDENCE.....ba room number bane kaman yadda aka saba a dakunan hotel. "Residence?" Ta tambaya tana duban fuskarsa sanda yake scanning key card dinsa. Yanaso yayi kaman baiji ba,amma sai.ya tuna,alqawari ya mata,duk da bai da tabbacin zai amsa kowacce tambaya tata. Yanaso LOKACI yayi.....LOKACI yake jira da zata gama sanin koshi waye.....zata san dukka tambayoyin dake kansa a zuciyarta,amma ya sani.....a abinda yake gani a idanunta tattare dashi,ba lallai ta iya kaiwa wannan lokacin haka ba. ZUCIYARTA yake fafutukar mallaka a yanzu.....dole ya cire duk wani burbushin rashin yarda da sake sakewa tsakaninsu. "Eh....residence.....It stays closed unless I’m in Dubai.” ya fada softly yana miqa mata hannunsa. Taku biyu ta qaraso,ta miqa masa nata hannun ya jata a hankali zuwa ciki. Zata iya kiran ginin da cikakken gida madaidaici wanda ha hada komai da komai. Madaidaicin gidan da idan kana ciki ba zaka dauka rayuwa kake cikin hotel ba. Private infinity pool,personal butler team,private dining area,ga panoramic dubai skyline view daya tafi da ita tun a kallo daya wata duniya ta daban. Ta gama sarewa.....ta gama sallamawa......a take kuma ta gayawa kanta "DA GASKE BAKISAN WAYESHI BA AKHNAN.....WUTSIYAR RAQUMI TAYI NESA DA QASA". Ta sake daga idanunta,komai na gurin yana gaya mata tabbas gurin mallakinsa ne. Kowacce iska da qamshin turarensa data sani take kadawa. Favourite coffee brand dinsa yana gurin,dakin ajiyar suturun da tana kalla tasan tabbas nasa ne....ga gurin sallarsa.....yana shirye da tsarinsa kamar wanda suka baro a gida,kaman yadda tsarin nasa na gida yake. "Ya Allah" Ta fadi jikinta yana wata irin mutuwa,saita koma gefe ta zauna a hankali tana jiyo motsin ruwasa daga toilet. Wannan sama da abinda tayi buri ne.....wannan sama da abinda ta roqa ne.....bama wannan ba kwata kwata. Batayi burin me dukiya ba......saboda tana ganin ta gada. Batayi burin me tarin dukiya irin wannan ba. Wayayye ta nema.....shi ta dinga lalube wanda zai tayata ta qara gina kanta. Wanda zai bata dukkan 'yanci. Amma a yanzun wani mutum a daban take gani,wani LU'U LU'U take hange wanda ya shiga cikin farin qarfe na azurfa yake rayuwarsa. "Anya bankai kaina inda akafi qarfina ba?" Ta tambayi kanta tana jin kamar tana narkewa tana zama qasqantacciya. Inde a abinda take gani ne ya tabbata...lallai babu ko shakka MUHAMMAD HAISAM yafi qarfinta ita AKHNAN MUHAMMAD HAMMUD fin qarfi na har abada. Anya kowa da kowa ma ya gama sanin wayeshi?,ko!yana binne kowa ne kaman yadda yaketa binneta?. "Are you okay?" Taji ya fada a hankali. Idanunta ta daga tana sake kallonsa,ya cire thobe dinsa ta sama,amma farar jallabiyyarsa na sake nuna kwarjininsa da haibarsa. *zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 08187255862 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 08187255862 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 93* __________________________ *_Amintaccen gurin siyayya_* *_ingantattun kaya akan ingantaccen farashin da ba irinsa a kasuwa_* *_BONONZA DA PROMO akai akai_* *dukka sai a HUGUMA CLOSET* *Duniyar kayan yara,mata,maza,dukka* *shaddodi,atamfofi,laces,abayas,jakankuna,takalma,agogo,sarqoqi,English wears,night wears,under wears,da duk wani nau'in sutura babba da qarami* *_Karki yadda ayi babu ke.....leqa kiga yadda closet din HUGUMA kullum ke cike da kaya akan farashi me kama da KYAUTA_* *_YAN SARI....YAN REPOSTING.....DA SARAKAN ADO MASU SIYA DON KANSU....DUKKA INA MUKU MARABA_*🤝🤝🤝🤝 https://chat.whatsapp.com/FrqgC0YmUWP4FPmUzYuLJX __________________________ Duk wani abu da takeji ko take qissimawa zata masa.....ko zata aikata da zarar ta kalli wadannan narkakkun idanun nasa saita kasa. Da zarar ta kalli qwayar idanunsa sai taji komai yana kwance mata. Batasan wanne irin baiwa ce dashi haka ba......batasan har yanzu a wanne aji zata sakashi ba. Abu daya ta sani,kowacce rana yana kan yiwa zuciyarta mummunae b'arna. Kowacce rana yana sake lalata tunaninta,yana sake sanya mata buri da kuma son kasancewa dashi. Hannun rigarsa da yake warwarewa ya saki yana takowa a hankali,ya iso gabanta,sannan ya tsugunna kamar wanda yake neman gafara. Kyawawan idanun nan nasa cikin blue eyes dinta,tafin hannunsa ya dora a nutse saman cinyarta,dumin hannunsa ya ratsa fatarta,ya kuma isa ga qasusuwanta ya ratsa jini da jijiya. "My healer?" Ya fadi yana karkatar da kansa gefe kaman wanda yakeson sake ganin fuskarta da kyau sama da yadda yake kalla yanzu. Da wannan salon na iya sarrafa harshe,cikin harshen French ya soma magana da ita da accent dinsa ke kai mata ko ina cikin jikinta. "Na sani,....na saka shakku da yawa a kaina cikin zuciyarki....amma ina me tabbatar miki ban boye komai wallahi don na cutar dake ba. Bansan ta yaya zan fahimtar dake komai ba.....bansan ta yaya zan miki bayani duka a dunqule lokaci daya ba,amma ina roqonki....." Sai ya dakata kadan,kamar yadda ta fahimci rarrabe magana a dabi'arsa yake,kuma duka yana cikin abubuwan dake sanyawa kaji idan ya maka magana,maganar tashi takai maka ko ina. "......ina neman alfarma......ki barwa lokaci ya miki bayanin waye ni. Abu daya zan iya gaya miki da kaina,ni muhammad ba macuci bane....ba kuma mugu bane......." Ya sake dakatawa yana kallonta "......zaki wannan alfarmar?,ni kuma zan amsa miki duk abinda kika tambayeni da haqiqanin gaskiyata" Ya qarasa fada muryarsa can qasan maqoshinsa. "La haula wala quwwata illa billa" Ta fada a hankali tana lumshe idanunta. Ita daya tasan yadda yake nasarar rugurguza zuciyarta. Ita daya tasan yadda maganansa ke samun nasarar narka mata zuciya. Ita daya tasan tasirin da komai nasa yake mata. Maganarsa.....kallonsa....kai daidai da wanzuwarsa kadai a guri yana ruguza mata dukkan lissafi. "Kinyimin?" Ya sake fada a hankali yana dora kuncinsa saman cinyarta yana leqen fuskarta. Kai ta daga masa a hankali yana kaucewa kallon fuskarsa,don da qyar take hadiye yawu saboda yadda gaba daya kwarjininsa ya cika mata guri. "Na gode" Ya fada a tausashe yana miqewa,ya dora lips dinsa saman goshinta yayi kissing sannan ya janye baya a hankali. Agogonsa ya kalla kadan sannan ya sake maida dubansa kanta. "Xakimin haquri na kwanaki uku zuwa sanda zanje gayyatar da akamin.....zan zama busy na kwanakin kadan.......Allah yasa hakan bazai bata miki rai ba" Kai ta kada a hankali,tunaninta ma Allah yasa shehnaz su iso da wuri,idan sun iso ma bata da matsala da yawa,suna da gurin zuwa sosai da zai debe mata kewa na kwanakin. "Na gode" Ya sake maimaitawa,daidai sanda na'ura ke shaida masa ga saqo daga kitchen. Bai jima da fita ba ya dawo,idanunsa a kanta. "An kawo abinci da komai da zaki iya buqata......" Kai ta girgiza a hankali. "Ba yanzu ba" Ta fada tana motsa labbanta a nutse. Idanunsa ya janye daga kanta ya fara cire cufflinks dinsa. Wani abu daya daya lura da ita,ba kowanne abinci takeci ba,ba kuma a kowanne lokaci ba. In fact ma gaba daya abinci kamar bai dameta ba. Idanunta ta lumshe a hankali sanda yake zare jubah din jikinsa. Zuciyarta na bugawa d'il d'il d'il cikin qirjinta. Wannan ginannen jikin nasa.....wada yake zagaye da muscles da aka ginu saboda daga qarfe shi ya bayyana. Qafafuwa hannaye dama qirjinsa gaba daya cike yake da gargasa dake da duhu da santsi. "Zanyi wanka" Ya fada softly yana dubanta hannayensa harde cikin faffadan qirjinsa. "A.....afito lafiya" Ta fada sautinta yana rarrabewa. Sanda ya bude daki daya cikin residence din bata kawo komai a ranta ba. Bata tuna zasuyi cudayya a komai ba...zasuyi tarayya a komai ba......kuma zasuyi mu'amala da komai a tare ba sai a yanzu. Sai a yanzu daya yaye mata wannan gangar jikin nasa dake matuqar mata kwarjini,wannan gangar jikin nasa da ba zaka dauka haka yake da cika idanu da ban tsoro ba idan bai budesu haka ba. "Care to keep me company in the bath?" Ya fada a nutse da french. Ba shiri ta bude blue eyes dinta tana waresu a kansa,saidai kuma a rude ta maidasu ta kulle tana kauda kanta. "Aah......" Ta fadi tana qarawa da girgiza kai. Dariya tazo masa a nutse,ya fiddata a boye. Da gaske yarinyace,komai nata sabo ne. Sai yayi raino da gaske.....sai ya mata wani karatu da yakeso daga macen aurensa. Rayuwar aure yakeso abar kwatance.....irin rayuwar da soyayya ba zata mutu ko tayi bacci ba. Rayuwar aure yakeso me kama da ALJANNAR DUNIYA ba rayuwar kidahumanci ba. Rayuwar aure yakeso da litattafan soyayya zasu gaza wajen rubutata daidai.....ba kalan rayuwar akeyi a kowanne gida ba. (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) Juyata da dorata akan wannan bigiren bazai masa wahala ba......amma dole yabi a nutse kuma a hankali. Ya taho da ita nan ne saboda ya daidaita zuciyarta daidai da yadda yakeso ta kasance. Ya daukota nan don ya bata hutu,ta huta sosai,irin hutun daya tabbatar ba lallai ta samu a gurin nanay ba. Ya daukota nan saboda su samu shaquwa da kusancin da ko lokaci bai isa ya shiga tsakaninsu ba. Ya yiwa kansa alqawarin bazai taba koda yatsarta da sunan neman wani abu daga gareta har sai da yardarta,amma hakan bazai hanashi yada manufarsa da sake dasa kansa a zuciyarta ba. "Is okay" Ya fada yana daga kafadunsa. Kai tsaye ya wuce bathroom din,wanda yake da wata irin qawatacciyar qofa da kuma toilet daban a ciki. Numfashinta da take riqe dashi ta saka a hankali tana juya idanunta. Bugawar da zuciyarta keyi take saurara. Dariya kadan ta qwace mata. Ita kanta dariya ta bawa kanta,yadda ta rude dukka sai a yanzu komai yake dawo mata "Kinga gymnastic guy ko?" Ta fadiwa kanta da kanta can qasan maqoshinta. Dariya kadan ta subuce mata,ta juya idanunta a hankali tana qarewa dakin kallo. Wani irin tsari da yanayi da dakin ke dashi,kamar kafin a ginashi sun shiga zuciyarta sunga tsarinta da zabinta a kaloli da tsarin daki. Ta fidda iska me sanyi a bakinta,abubuwa da yawa suna mata yawo akai. Duk inda wayewarta.....ilimi da yawan dukiyarta yakai,a yanzun tana jinta wata maqasqanciya kuma baqauyiya idan har tana tsaye a gabansa,idan har tana cikin duniyarsa......idan har tana cikin da'irarsa sai taji komai nata yana zagwanyewa. Wannan tunanin ta watsar,don ta tabbatar bata da riba a ciki sai sake dilmiya cikin qaunarsa,sannan ba abinda zai amfanar da ita face ta zama baqauyiya zam kamar yadda hotel din yake shirin maidata cikin qasa da minti arba'in kawai. Komai na musamman ne....komai na dabanne,komai kuma da nasa tsarin cikin hotel din. Especially mr aba jifar residence din. Karon farko kenan data gani da idanunta,bawai a labari ba. Residence guda cikin hotel din da yafi kowanne hotel tsada a duniya?. "Wanne irin arxiqi ya mallaka?,me yasa baya qoqarin nunawa duniya kanshi?,me yasa silently power dinsa take magana?" Ta yiwa kanta dukka tambayar yana qoqarin lalubar number shehnaz ta kira kota WhatsApp,duk wadda ta samu. Shuru dakin ya dauka,sai qarar zubar ruwa a hankali daga bathroom din. "Akhnaaaannn" Kalmar ta fito da wani irin sauti tana sauka a kunnenta ta gauraya da shurun da dakin yayi. Haisam ne.....sautin ya fito can qasa amma ya mata wani irin tasiri a gangar jikinta. Kanta ta daga a hankali tana duban qofar bathroom din. Bashi ya bayyana ba,muryarsa ce kawai. "Hmmmm?" Ta fada a hankali. "Can you bring me the towel?" Ya fada da tattausan French dinsa dake dake tsumata. A duk sanda zai magana dashi sai taji wani abu cikin zuciyarta da kanta ya motsa. Girarta tadan tsuke kadan,me ya hada da bashi towel indai ba neman tsokana ba?. Idanunta ya sauka cikin nasa sanda yadan leqo da idanun nasa,wataqila yanason yaga yanayinta ne. "Mantawa kayi baka dauka ba?" Ta fadi a shagwabe,tana son dauke idanunta daga lallausan gashinsa dake digar ruwa,ya kuma kwanta sosai a gefan fuskarsa,hakan sai ya zama kamar wani ado na musamman ga kyawunsa. "Apparently" Ya fada idanunsa suna lumshewa suna bude kansu kusan lokaci guda,akwai wani siririn abu cikin muryar tasa,kaman yana amsa mata ne da nishadi,irin nishadin da mutum keji a duk sanda zai tsokani wani. "this French man....." ".......and his endless tricks" Ta fada can qasan maqoshinta tana kyabe fuska a shagwabe. Idanunsa ya sake lumshewa,ta masa kyau.....wani irin kyau da shagwabar tayi mata,yana jin kamar ya hadiyeta ya huta.....ko ya zauna ya lashe kayarsa tas.....saidai yanzun ba irin wanna kusancin yake nema ba. SABO yakeso.....sabon da zata nemeshi cikin kowanne motsi na rayuwarta. Kusanci zukata first kafin na gangar jiki. Miqewa tayi a hankali ta dauki towel din dake ajiye hannun kujerar daya cire kayan nasa. Da alama ya daukoshi dinne ya manta,sai wannan ya bata nutsuwa kadan,ta kuma sakejin nutsuwa sanda ta isa bakin toilet din taga kanshi baya nan kamar dazun. "Ga towel din" Ta fada tana dan daga murya kadan. Hannunsa taga ya zuro,tabi fararen dogayen yatsunsa da kallo wadanda ke digar da ruwa. Miqa masa towel din tayi saitin hannunsa,sai ya matsar da hannun gefe. "Gashi fa a ta nan" Ta fada tana sake cuna masa,saidai ya sake kaucewa gefe,kawai saita yanke shawarar kama hannun nasa ta saka cikin towel din. Wanda ya rigaka kwana dole ya rigaka tashi,sanda ta kama hannun,sai yayi amfani da wannan damar ya damqe yatsunta cikin nasa,ya kuma hade da ita da towel din ya jawosu cikin softly gaba daya ya maida qofar ya b'ameta b'am da lock. "Haisam!" Ta kira sunansa a rude tana ware blue eyes dinta a kanshi. "Oh my god.....say it again?!" Ya furta yana cusa yatsunsa cikin jiqaqqen sumarsa yana maidata baya saboda hana mishi kallonta sosai da takeyi. Idanunta ta janye da sauri tana duban qofar yadda ta rufe,gaba daya bathroom din ya cika da warm steam da qamshin turarensa. Bugawa zuciyarta kawai takeyi,ta kasa kallonsa.....ta kasa daga idanunta ta kalleshi,baida maraba da mutumin daba komai a jikinsa. Da wani irin shauqi dake fusgarsa ya tsaya a gabanta idanunsa a kanta,sanye cikin relaxed black swim pant da gurare kadan ya lullube a jikinsa,gashinsa dukka a jiqe yake daga na jikinsa har na kansa,yana digar ruwa a hankali. "You were leaving too quickly" Ya fada da wata kasalalliyar murya yana sake samun kusanci da ita, *zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 08187255862 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 08187255862 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 94* _________________________ DEA’S MODEST ARTISTRY ✨ Aminataccen wajen samun ✔️ Abaya masu kyau ✔️ Lifaya & Veils masu tsari ✔️ Handmade paint work ✔️ Shadda designs ✔️ Elegant modest wears ✔️ Accessories masu kyau da inganci Muna kawo muku kaya masu kyau, tsafta da araha domin kowane irin event 💫 Ko na daily wear, outing, wedding ko special occasions — DEA’S MODEST ARTISTRY na tare da ke 🖤 📍Quality first 📍Affordable prices 📍Neat finishing 📍Classy & Modest styles Ki kasance cikin kyau da nutsuwa ba tare da tsada ba ✨ https://chat.whatsapp.com/IZGMwJXP8Oa5qUc4sDSKZv?s=cl&p=a&mlu=3 __________________________ Hararsa tayi wannan karon,hararar data dauki hankalinsa matuqa. Bai taba sanin harara na yiwa idanu kyau ba.....mugun kyau me fusgar hankali ba sai yanzu. "Ka yimin wayo ne kawai....dama ka shirya hakan" Ta qarasa maganan a shagwabe tana narke masa. Dan tattausan murmushi ya saki yana duban wadannan unique blue eyes din nata. "Yes" Ya furta kansa tsaye "And I’d probably do it again.” Kanta ta girgiza,saita rabashi tana niyyar wucewa zuwa bakin qofar fita. Softly ya tare hanyar,bada qarfi ko nuna iko ba,sai wani irin teasing closeness yana lalubar qwayar idanunta "One minute mana" Ya furta yana karyar da kanshi. "Haisam" Ta sake fadi cikin subutar baki ganin ya fara narke mata irin yadda ya saba. Wannan narkewar da take tuna mata amanar nanay ce shi a hannunta.....wannan narkewar da take sanyata jin kamar ta gaza kula dashi yadda nanay tace tayi. Sunkuyawa yayi kanta kadan,ya lalubi kunnenta,sannan a hankali kamar me rad'a yace. "You called me a gymnastic guy earlier" Dam zuciyarta ta buga,ta zaro dukka idanuwanta waje,wata irin kunya tana qoqarin narkar da ita. "Ban fada a gabanka ba!" Tayi furucin cikin mamakin yadda akayi yaji. Dariya taso qwace masa,a komai yarintarta ke bayyana. Maimakon ta qaryata ko tayi qoqarin kare kanta...amma sai ta bashi wani hint daya tabbatar masa ta fada din. Sautin dariyarsa kadan ya bayyana,still muryarsa cool yace. "Your face did" Bata da sauran zabi,sai kawai ta saka tafukan hannunta ta rufe fuskarta cikin wani nauyi da kunya. Da murmushi yake kallonta tana dada burgeshi,sai ya sanya hannunsa ya cire hannayen nata daga fuskarta gently "Relax" Ya fadi a nutse. "I just wanted a little more time with you". Ya fadi kaman yana bata daman zabi. Wani irin shuru ya sake ratsa tsakaninsu,tana iya jin yadda zuciyarta ke zillo a qirjinta,kamar tana gaya mata cewa. "Please.....stay with himmmm" . Shurun yaci gaba da wanzuwa,bai sakar mata hannuwa ba suna cikin nasa softly,hakanan steam din bathroom din yaci gaba da zagayasu yana ratsasu dukkaninsu. Bayaso tace NO don haka ya mata riga malam masallaci,towel din ya miqa mata sannan yace. "Before Nanay somehow appears in my imagination again and ruins the moment.” sai ya hade da hannunta ya dagata sama cak yana nufar bathtub da ita. Duk da a dan tsorace take amma magananshi na qarshe ya bawa akhnan dariya. "Ka tsorata da mommy na ne?" "I’m simply protecting my peace" Ya fada sanda dukkaninsu suka tsunduma cikin bathtub din ba tare daya damu da kayan dake jikinta ba. Minti goma sha biyar ashirin talatin har arba'in kafin yakai zuciyarsa nesa su fito daga wankan. Bai mata komai ba......amma yayi warming up nata sosai,har bata iya hada idanu dashi. Yaja mata stool ta zauna,tana jin towel din da take daure dashi yayi qanqanta da yawa,sai mutsu mutsu take tana qoqarin rufe cinyoyinta. Inda Allah ya taimaketa towel din daya dora mata saman kanta don goge danshin gashinta dashi ta rufe kafadunta zuwa saman qirjinta,duk da bai rufu ba gaba daya amma yafi babu. Ta dauka zai maza ya shirya ne,amma sai taga ya jawo daya stool din ya dasa a gabanta,ya kuma hau kai ya zauna da nasa towel din da iya gwiwarsa kawai ya tsaya. Ya zuba mata wadannan shanyayyun idanun nasa da suka sake tsumuwa,cike fal da shauqin soyayyarta da sha'awar kasancewa da ita. Kasa jurewa tayi,kashe mata jiki itama yakeyi,ga wani warm light da dakin yake bayarwa yana sauka a jikinsu softly. Ko blinking idanunsa bayayi sosai,kaman ya manta da komai dake cikin duniya. Ta motsa kadan tana tattara kalaman bakinta. "Me kake kalla haka?." Shuru kaman bazai amsata ba,sai idanunsa still dake biye da ita da wata irin nutsuwa me nauyi. "You"ya furta softly. Zuciyarta taji ta harba,saita dauke idanunta da sauri yanayin yana mata nauyi,ta kasa jurewa still,yana sake narkata tare da kaita wani gejin da bata zata zatakai akan kowanne dan adam ba "Karkamin irin wannan kallon...." Tattausan murmushi ya subuce masa,ya sake rage tazarar dake tsakaninsu ta hanyar qara matsowa. "Wanne irin kallo?" Ya tambaya kaman baisan komai akai ba. Kanta ta girgiza a tausashe. "Kamar zaka karanta duk abinda ke raina" Ta furta masa tsoronta.....tsoron daya dade da karantarsa ta cikin qwayar idanunta. "Maybe I'm trying to" Ya motsa lips dinnan nasa masu sulbi yana furta kowacce kalma a nutse kaman mai lissafa adadinsu. Da tsoronsa kadan da mamaki ta waiwayo,suka hada idanu,murmushin da bata shiryawa ba ya kufce mata a tausashe,abinda yasa ya qara jin kallonta kawai shine abinda yafi buqata a duk duniya a yanzu. Hannunta ta daga tayi waving gaban fuskarsa. "Haisaammm....."da murmushin kunya akan fuskarta. ".....blink manaaa" Ta qarasa fada tana jan kalmar qarshe din. Murmushi ya saki yana kama yatsunta. "Ki qyaleni na kalli halal dina.....kinsan darare nawa na kashe ina kasa bacci saboda wannnan?" Ya fada yana nunata daga saman kanta har zuwa qafafunta. "Ban taba kalla a wajen wata 'ya mace ba.....so please....let me....." Sai ya kasa qarasawa yana hadiye wani abu da taga wucewarsa ta adams apple dinsa. (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) Idanunta take sake shirin daukewa,sai maganansa ya dakatar da ita. "You look beautiful when you're trying not to look at me" Ya sake jefata cikin wata kunyar,kawai saita rufe fuskarta da hannunta data samu ta zame daga cikin nasa. Abinda yakeso ya fara samu,don haka ya sake matsawa dab da kunnuwanta,har fatar jikinsa tana gogar tata,cikin kwantaccen sautin nan.....da sound dinnan.....da muryar nan data zama sirri a tsakaninsu "And that makes it difficult to stop staring.” "Wayyo Allah momma na" Ta fadi tana jin wani abu yana narke mata,saita tafi kawai ta kifa fuskarta saman dressing table. "The beginning" Ya fada can qasan zuciyarsa,wannan dangerous smile din yana fita daga kan fuskarsa,ya cije lips dinsa na qasa kadan,sannan ya miqe a nutse daga saman stool din,ba tare daya sake matsa mata ba ya wuce don shiryawa ya barta a gurin tana narkewa kaman ruwa. Tunda ta shirya tana zaune ta kasa daga kanta ballantana ta kalleshi. Tana iya ganin gilmawarsa da motsinsa har ya kammala nasa shirin "Na gama.....zan fita" Ya fada idanunsa a kanta, Maganar tasa ta sakata daga kanta,saidai tayi nadamar kallon data masa. Wani irin kyau me sunan kyau yayi. Ya narke da wani sassanyan kyau cikin shigar suit din da wannan shine karo na biyu data taba ganinsa da ita. Wannan sumar.....wannan sajen da yafi zubi da tsarrariyar qasumbar da aka aske aka yiwa wani style din shape daga kuncinsa zuwa habarsa......wadannanmanyan fararen idanun gaba daya sun hadu sun haska cikin kalar suit din jikinsa. "Ina zakaje?" Ta zaqulo tambayar da qyar saboda bataso ya fahimci wannan kallon qurillar da tayi masa a yanzun. Hannunsa ya miqa mata,ta riga ta soma sabawa da irin wannan abun nasa,saita dora nata akai. Ya kuwa tasheta tsaye yana qare mata kallo,duk da ba wani kayan jan hankali ta sanya ba,amma yana jin kamar ya cinyeta ya huta. "You look beautiful so ma sha Allah" Ya fada softly yana kissing forehead dinta. Qugunta ya riqo yana janta cikin jikinsa. "Muje ki rakani,ko.iya bakin reception ne......" "Baka ban amsa ba" Ta fada tana jin wani irin nutsuwa da wani garkuwa da take samu a duk sanda dumin jikinsa ya ratsa nata. "Zanyi concerning wasu papers wa me gidana ne" Ya fada yana hana idanunta haduwa da nasa. Dubansa take da zara zaran eyelashes dinsa,ya saki murmushi kadan yana miqa yatsansa ya tabasu,saita dauke kanta gefe. Wani yanayi ne daya karanci tanaso tace masa bata yarda ba amma ta kasa fadin hakan. "I won't be long......" Ya fadi yana sake mata murmushi sanda driver ya bude masa qofar Rolls Royce din data masifar daukar hankalinta. "Try not to miss me too much" Maganan data sauka da nauyi da kima a cikin ranta,ta mata kuma rakiya sanda take komawa ciki da wani irin yanayi me tattare da shauqi. "Too much" Ta maimaita a cikin kanta. Ya sani ma kenan..... Yana san dole tayi missing nasa?,abu daya kawai ya roqa.....kada tayi missing din nasa da yawa. A hankali ta waiwaya,sai idanunta suka hange mata wasu motoci daban suna rufawa tasa baya. Kenan ya zabi ya nuna mata iya rolls Royce ne kawai?. Idan ta lura da kyau royal escort ne suke biye dashi. "Wanne irin rayuwa yakeyi ne a bayan ido na?" Ta tambayi kanta tana ci gaba da wucewa ciki a hankali. Idan baya gabanta......sai taji tarin tambayoyi da takeson masa......amma da zarar ya wanzu a gabanta sai taji kanta yayi blank......sai taji ba wata tambaya data rage mata. Residence din nasu yayi tsit sosai,sai ma'aikata dake sake gyaran gurin da take hanga d'aya d'aya,kaman sunzo ne don su dawwama cikin hotel din. Ta bude qofar dakin a hankali tana cire takalmanta. Takalmin da tunda ta sanyashi a qafarta take sake qare masa kallo saboda sanin ainihin kudinsa. Idanunta ta maida cikin dakin,komai na dakin yana dauke da wanzuwarsa. Turarensa.....agogonsa daya bari....cufflinks dinsa dake saman table.....ga half finished coffee din daya fara sha ya bari bai qarasa ba. A hankali ta zauna gefan sofa din,inda ya zauna a dazun kafin ya tashi,ta miqa hannunta ta dauki cup din coffee din. A bakinta ta sanya a hankali,hancinta ya zuqo mata qamshin coffee din da qamshinsa wanda komai ya taba koda sau daya ne tak sai yabar masa wannan tambarin na ya taba mu'amalantarsa. "Yabar dumi a komai" Ta fada a hankali tana murmushi tare da cire cup din ta ajiyeshi,tana jin yadda gangar jikinta ta fara canzawa. "Shin da gaske ina missing dinsa?" Ta tambayi kanta da kanta. Kanta ta girgiza da sauri tana musanta zuciyarta. "Ridiculous" Ta fada tana yatsina fuskarta. Telephone dake ajiye a parlor ce tayi qara,ta miqe a nutse taje ta dauka. Daga ma'aikatan sashen ne. Suna tambayarta ko akwai wani abu da take buqata?. Tace musu ba komai ta maida wayar ta ajiye. *zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 08187255862 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 08187255862 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 95* _________________________ *_Amintaccen gurin siyayya_* *_ingantattun kaya akan ingantaccen farashin da ba irinsa a kasuwa_* *_BONONZA DA PROMO akai akai_* *dukka sai a HUGUMA CLOSET* *Duniyar kayan yara,mata,maza,dukka* *shaddodi,atamfofi,laces,abayas,jakankuna,takalma,agogo,sarqoqi,English wears,night wears,under wears,da duk wani nau'in sutura babba da qarami* *_Karki yadda ayi babu ke.....leqa kiga yadda closet din HUGUMA kullum ke cike da kaya akan farashi me kama da KYAUTA_* *_YAN SARI....YAN REPOSTING.....DA SARAKAN ADO MASU SIYA DON KANSU....DUKKA INA MUKU MARABA_*🤝🤝🤝🤝 https://chat.whatsapp.com/FrqgC0YmUWP4FPmUzYuLJX ___________________________ Cikin mintuna taji kadaici yana neman kayar da ita,sai kawai ta sake laluban shehnaz. Bugu biyu ta dauka,saidai karadinta shine abu na farko daya fara cika mata kunne. "Kee!!!!!...wai mu zakiwa surprise ki rigamu isa dubai?" Dariya kadan akhnan tayi amma mamaki yana cikata. "Ya akayi kika gane?" "Latsani......bakiga line dinki bane?,kinsan me yake rubutawa kuwa?" Idanu tadan waro waje. "Ban gane ba.....me yake rubutawa shehnaz,banason sharri". "Ba sharri take ba....ni kaina nasan yanzun saimun lallaba zamu dinga samun ganinki" Muryar aisa ta maye gurbin muryar. Tashi tayi ta zauna sosai tana fidda blue eyes dinta. Tayi kewar aisa ba kadan ba,har batasan adadi ba,ta jawo pillow din da sai dayazo jikinta ta tuna pillow din da haisam ya rungume ne a dazun,qamshinsa ya cika mata hanci. "Nayi fushi....nayi fushi" "Na yarda....kome zakice.....amma ki jira gobe mu iso,sha biyu na rana agogon dubai in sha Allah". Qaramin ihu ta saki,har tana jin kamar tayi tsalle ta kamosu. Hira sosai ta barke a tsakaninsu. A cikin haka suka gaisa da ahmad,ahmad din da duk bayan kwanaki biyu rakkin saiya kirata. Suka gaisa da Nannie,sannan morsa safiyya da haka kawai takejin wani nauyinta da respect yana ratsata. Taso ta danyi mamakin abinda ya hadasu haka guri daya amma sai bata tambaya ba. Ta nema sultane,kaman yadda suka saba akace mata yasha magani ya kwanta, "Ya ahmad......seven days ba tare da naji muryar sultane ba.....haka aure yake?" Ta fada a karye. Wani dariya yasaki mata. "An ture gwamnatinki ne wasu sunhau yarinya" Ya fada da tsokana a muryar sa. Raurau tayi da idanu,kafin tace komai taji muryar morsa safiyya,da alama wayar ta karba. "Kada ki biye masa biftuu,ko dasu sultane yace zai kiraki,magani yasha,wani magani yake sha wanda yake yawan sakashi bacci,amma yau dinnan zan tabbatar kunyi magana" Ta fada tana qoqarin boye hawayenta da kalar raunin da zuciyarta tayi. "Na gode momma.....na gode". Sunyi hira sosai har ta wasu awanni kafin suyi sallama. Duk sai taji zumudin zuwan nasu yana cikata. Ta soma dawo da wasu memories,zuwansu dubai a sanda bata da aure. Suna matuqar son zuwa,saboda qasar na musu dadi da cikakken tsaro da 'yanci. Falaak ta shiga nema,wanda ba jimawa ta shiga ta daga. Muryarta kamar alamun bacci take,amma koda taji muryar akhnan din sai gata ta wartsake. "Yaa biftuu.....kin daina fushin dani?" Falaak ta fada a narke. Wani murmushin kunya akhnan tayi. Ta tuna wancan ranar.....wancan lokacin,amma a yanzun sai taji zuciyarta ba wannan haushin na falaak. To haushin me ma zataji nata?,bayan abinda tayi itama ya biyo ta kanta?. "Ni ba haushinki nakeji ba falaak,tausaya miki nayi kuma baki gane ba" Dariya tayi kadan tana cewa "Inaso na kiraki.....amma tsoro nake" "Ni gashi yanzu na kiraki ai". Hira sosai tsakaninsu,irin hirar ma da bata dauka zasuyita ba. A cikin hirarta da falaak ta dinga tsintar abubuwa da yawa. Da alama yarinyar ta iya abubuwa masu yawa,a hankali daga waya sai gashi sun koma chart da ita ta watsapp. Awa daya da rabi suka shafe kafin su rabu ya chart din. A awa dayan ta d'arsa mata son koyon abubuwa da yawa,a awa dayan ta dauki wasu lesson da tayita tunanin ya akayi falaak din ta fita fuskantar rayuwa haka?. "Momma ce ta raineta.....mammina ce ta raineki" Amsar da zuciyarta ta bata kenan. Amsar data zauna ta yita jujjuyata,ta dinga kawo abubuwa da yawa a ranta. "Anya?" Karo na farko zuciyarta taji ta dasa wata qatotuwar ayar tambaya akan mammina din.....karon farko da taji tana sake nisa da ita a zuciyarta nisa me tarin yawa. Batasan adadin mis calls nata guda nawa ke a wayarta ba,daga sanda tabar agadez har zuwa wancan satikan. Wasu kiran a gaban idanunta suke shigowa su kuma yanke su koma mis call,amma ko sau daya bata taba sha'awar dagawa ba ko kuma tabi kiran. A hankali hankalinta ya soma karkata yana komawa kansa. Ta soma lissafin wucewar kowacce daqiqa da mintuna zuwa awanni. Rana ta fara karkata zata fadi,sai ta yanke fara alwala saboda kiran sallar daya fara daga cikin wayarta. Idanunta ta lumshe tana jin wani dadi da nutsuwa yana ratsata. Bata saka kiran sallar ba,amma ta sani shine ya sanya. Yana da qoqarin kiyaye lokutan ibada matuqa,daya daga cikin abinda ke qara masa kwarjini a idanunta kenan. Da yawa sallarta da wasu zaman addu'o'i ta fara daukar yanayin nasa ba tare data sani ba. Cikin bathroom din tayi alwala ta tayar da sallar magariba a musallah din dake dakin. Data idar kiran falaak ya shigo mata. Nan ta zauna tana sake cikata da surutu kafin kuma tace. "Maleekqalb ya kusa dawowa.....zanje na shirya yaa biftuu" "Yayi kyau" Ta amsa mata a taqaice. Wayar ta ajiye tunaninta yana tafiya wani guri. "Kenan kwalliya zata masa sanda yake dawowa daga wani guri?" Sai taji kaman saqo ne falaak ta aike mata,ta miqe a nutse tana tayar da ishai bayan da wayarta ta sake bugawa. Samun kanta tayi da zare kayan jikinta ta daura towel. Wani ra'ayi taji yana saukar mata......ta gwada wani abu itama,ko sau daya ne ta gani ko zata burge?. Bathroom ta wuce ta bata lokaci tana wanka,bawai don akwai buqatar yin wankan tare da ita ba. Ta fito steam din bathroom din yana yawo a hankali. Ta tsaya a gaban babbar luxury closet din dake cike da kayan da suka bata mamaki. Tun asali suke zube a jere a tsare haka a ciki?,ko kuma dama yasan ya shirya tahowa ne da ita?. Abinda yaf bata mamaki,komai ta taba cikin kayan sai taga favourite dinta ne,tun daga color zuwa design gaba daya. "Ya akayi ya sani?" Ta tambayi kanta,sai taji can qasan ranta tana ganin baike da aibun kanta. Ta kasa riqe abu daya da nanay ta gaya mata tattare dashi,duk wani leakage a kanshi ta gaza haddaceshi. (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) "Me yasa ya damu dani da komai da nakeso?" Ta kuma fadi sanda take sake qarewa kayan kallo. Silk abayas,soft fabric....elegant sleepwear......ga wasu luxury perfume masu yawan da batasan adadinsu ba,kamar kwasosu kawai akeyi ana zubawa(batasan gidan turaren ta tarar ba). "Wanne ne zaisa ya kasa dauke idonsa daga kaina?" Karo na farko da taji tanason yin abu don ta burge wani,wanin ma wai d'a namiji da basa cikin lissafinta. Dariya ta yiwa kanta,kafin ta saka hannu ya ciro wata soft royal silk abaya. Soft champagne gold color me wani irin taushin kallo a idanu. Lokaci ta bata sosai ta shirya kanta da wanin irin yanayi da taga birra na mata. Hannunta dukka taji sun gaji ko kafin ta gama gyara gashinta,saidai ko ita kanta data gama styling nasa sai data sake kalla cike da mamakin ita tayi wannan gyaran?. Ya kwanta ta gaban goshinta kadan,ga wani soft waves kadan. Haka kawai tayi sha'awar sauya turare yau saboda tarin turarukan data gani a gabanta. Kowanne idan ta dauko sai ta bude idanunta waje saboda tsadar duk kwalba daya. Abinda yafi daure mata kai shine.....duk favorite brand dinta ne "Bai manta ba a wancan ranar dana gaya masa?" Ta fada qasan ranta. Murmushi ya subuce mata,a karon farko da taji wani aminci da yarda da son da yake mata,duk da bata taba kokwanto ba.....amma na yau din na dabanne. Vanilla oud and rose musk tayi amfani dashi,qamshin da ita kanta taji ya tafi sosai da ita. Sanda ta kalli agogo sai taga lokacin ya mata tsayi qwarai daga sanda ya fita zuwa yanzun. Wayarta ta dauka ta juya tana fita saita yanke wucewa inda zata iya ganin panoramic views na dubai. Tana tsaye gaban panoramic glass window din. Sosai take ganin dubai skyline din tana qyalli da haske a gabanta kamar taurari masu rai. "Beautiful but lonely" Ta fada a hankali tana jin yadda gurin yayi mata. Su shehnaz ta tuna a irin wannan lokutan sukan kasance tare. Suyi hotuna da videos su ajiye a matsayin memories kafin dawowa ta gaba. A hankali ta sake komawa tunaninsa,muryarsa nakai kawo cikin kwnayarta. Royal suit din yayi shuru amma muryarsa ta gaza tsaiwa a cikin kanta. "Yaushe na fara jin rashin wani mutum haka a kusa dani?" Ta tambayi kanta a hankali tana bude idanuwanta gaba daya gami da saukesu can qasa wadda keda nisa da inda take tsaye,saidai hakan baya hanaka ganin movement na ababen hawa. Tana shirin dauke idanunta wani convoy na black luxury SUVs ya shigo hotel entrance din. A nutse take bin tsarin motocin nasa da kallo wanda ke motsawa zuwa ciki da wata irin nutsuwa. "Haisam" Harshenta zuciyarta dama gangar jikinta gaba daya suka furta a lokaci guda. Kasa motsawa tayi a gurin,zuciyarta na qarfafarta ta fita ta tarbeshi kaman yadda nanay ta koya mata.....wata zuciyar kuma najin kunya da nauyin hada idanu dashi suna danneta. "Zan iya....zanyi" Ta gayawa kanta ta soma takawa a hankali tana fita zuwa bakin qofar farko ta suit din nasu. Ba gajiya kawai yakeji a jikinsa ba.....harda wata irin kewa da matuqar buqatar kasancewarsa a gefanta. Daga bakin residence din suka dakata,yaci gaba da takawa a hankali da waya a kunnensa yana sauraren bayanan balaraben daketa son saka hannun jari me yawa cikin sabon kamfanin turaren. A yau yaso su hadu dashi su gana shima,amma yawan ayyukansa na yau din bai bashi wannan damar ba. Sanda ya murda handle din yaji kaman bashi kadai ya murdashi ba,amma saboda hankalinsa yana takan wayar bai kawo komai a ransa ba ballantana ya kawo cewa itace. Daskarewa yayi gaba daya sanda qofar ta yaye,qofar data zama hijabi qwaya daya tsakaninsa da akhnan din *zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 08187255862 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 08187255862 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 96* _________________________ *_SHUWA INCENSE AND MORE_* 😊 *_kai daga jin sunan basai an gaya maka ba_* *_kai daga jin sunan basai ka tambaya ko tsaya tunanin maganar me ake ba_* *_MAGANA CE TA GIDAN QAMSHI_* *BAFA GAMA GARIN QAMSHIN DA KIKA SABA JI BA HAJJAJU* *KINA QONA TURARE YANA QAURI* *KINA SAKA KHUMRA TANA BIN SHANUN SARKI* *WANNAN DIN TURARE NE DAKE DAWWAMA A DAKI DA JIKI.....DA SALON QAMSHIN DAKE MANTAR DA ZUCIYA DUK WANI B'ACIN RAI* *TASTED AND TRUSTED👌👌👌100% HAJJAJU* *NA DABANNE A CIKIN NA DABAN*🙌🏽🙌🏽 *idan akazo kan SHUWA INCENSE an tashi magana* *idan ma kinsan baki shirya jan magana ba a duniyar qamshi to kisha zamanki hajajju* *_zaku iya magana da ita kai tsaye ta wannan number wayar_* +234 704 229 3387 __________________________ Wayar hannunsa ya sauke a hankali kamar wanda hannun nasa yake masa ciwo....kamar kuma tana shirin zamewa ta fadi daga hannunsa,idanunsa suka tsaya kyam a kanta. Wani irin kallo yake binta dashi kamar mayunwacin zakin da yaga danyen nama. From head to toe,irin kallon nan da ake kira da kallon qurilla,kallon da babu wani sashe daya bari na jikinta ba tare daya sauke Idanunsa a kanta ba. Silk kayan jikinta da sukabi jikinta suka lafe suna sake fidda calm aura dinta. Yadda ta kasa daga qafa haka ya kasa qara taku ko daya ne don ya isa gareta. Idanun nan nasa dafi suke zame mata,wanda zaita jagwalgwala zuciyarta cikin dare,yana sake lallasa naman zuciyarta da zallar soyayyarsa. A duk wunin daya mata irin wannan kallon......tana rasa baccinta a wannan daren gaba daya. Sanda dukka idanuwa ke bacci....ita nata idanun sukan kasance a bude ne cikin bege da ganin gilmawar kowanne motsi da irin kallon daya dinga binta dashi "What?" Ta tambaya a hankali tana motsa siraran labbanta dake glowing din lip gloss din data shafa dan kadan. Shuru yayi na wasu sakanni,kamar ya manta yadda ake magana,kafin a hankali muryarsa can cikin maqoshinsa yace. "......You cannot wear something like this and expect me to think normally khadeejaah." Ya qare da furta sunanta da wannan muryar da sautin dake tafiya da ita. Kunya taji ta rufeta,kunyar data bayyana sosai ta kuma zame mata wani irin ado daya sake burgeshi yaji kaman yana narkewa a gurin. "Its just an abaya fa?" Ta fada tana juya idanunta,ba don tayi calling attention nashi ba,kawai yanayin maganan ne yazo mata a haka. "No" Ya fada da sauri jin wani abu yana fusgarsa zuwa gareta "On you......its a problem" Ya cire qafafunsa yana matsowa inda take. Burinsa shine kawai ya isa gareta,burinsa shine kawai yaji duminta cikin jikinsa.....burinsa kawai yaji fatarta cikin tasa. Matso da ita yayi cikin jikinsa sosai,yana mata kyakkyawar tarba. Kyakkyawar rungumar data sanyata sakin ajiyar zuciya ba tare data shirya ba. Tana jin hannunsa yana yawo tsakanin kafadarta zuwa yatsunta yana murza silk din rigar cikin hannunsa tare da fatar jikinta. Sannu a hankali ya cusa kansa tsakanin wuyanta da kafadarta yana shaqar daddadan qamshin vanilla oud din da take fitarwa,muryarsa a rikice yace. "And.....this scent" Sai ya dakata yana sake zuqe qamshin sosai dake aike saqo cikin kwanyarsa. "......you're trying to destroy my peace tonight" Ya qarasa maganan yana dagata daga jikinsa yana kuma sarqe qwayar idanunsu guri daya. Kunya sosai.....kunyar data sanyata ta zabi kwantar da fuskarta cikin qirjinsa,tayi kuma kyakkyawan gamo da wannan qamshin nasa. Na musamman ne tabbas wannan qamshin. Duk yinin da zaiyi a jikinsa......bata taba ji wani abu ya jirkita qamshin ba,saidai ya sakeyin wani irin sanyi me kwantar da zuciya. Tana jikinsa suka qarasa ciki,har a sannan tana satar kallonsa. Har yanzu wannan kyan da suite din suka masa kafin ya fita shine dai. Nauyin aiki kujiba kujiba duka basu jirkitashi ba. Yanayinsa wani abune da ba komai bane ke saurin jirkitashi. Sai ta tuna........yadda yake magana calmly......yadda baya nuna dukiyarsa......yadda yake zama kamar ordinary mutum a gabanta......alhali......mutum ne da manyan mutane ke miqewa saboda shi. Batasan kallonshu take ba sai da yace da ita. "You waited awake......thank you" Ya fada yana cire agogon hannunsa idanunsa a kanta. Kasa amsawa tayi,don har yanzu zuciyarta tana processing komai a kansa. Taku biyu ya qara ya matso kusa da ita. "What's it?" Ya furta yana shafa gefan fuskarta da lallausan tafin hannunsa. "Wadanne mutane ne wadancan na daxun?" Wani faint smile ya taba lips dinsa. Kamar ya fahimci inda tunaninta ya dosa "Business associates" Ya amsa mata a hankali. "No" Ta fada har cikin ranta,haka kawai taji bata gamsu da amsarsa ba. "....people don’t look at ordinary businessmen like that.”. Magananta ya sauka kunnensa a hankali,shuru ya ratsa na wasu sakanni,sai ya sake takowa yana sake riga tazarar dake tsakaninsu sosai da wani irin kusanci,don har yanzu bai shirya bata license na sanin waye haisam in full details ba. Da wani irin low voice ya kalleta. "And yet....." Ya fada yana kulle idanunta cikin nasa. "…you still look at me like I’m only Haisam.” kasa magana tayi,yana sake dora mata kunyarsa. Batasan adadin yadda take kallonsa ba,ita kanta kamar idanunta sun rasa control haka takeji. Murmushi ya sake mata dan kadan,saidai zurfinsa a zuciyarta yana da yawan gaske. Yakai hannunsa yana dan janye mata gashin kanta daya sauko kaman zari rufe mata ido. "I think that’s my favorite thing about you.” (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) Tanaso ta tsaida kallonsa haka,amma abubuwan mamaki yake bata episode episode. Tayi tsam da ranta tana duban inuwarsa ta gefe kamar tana qoqarin hada mutum biyu guri guda. Haisam din dake mata magana cikin laushi......karyar da kai da karya matsayinsa. Haisam din dake iya roqonta.....haisam din dake iya bata haquri.....haisam din dake koma mata tamkar qaramin yaro. Da kuma mutumin da manyan mutane ke rusunawa.....mutumin da manyan mutane ke biye dashi a baya.......mutumin da manyan mutanen ke rakashi har bakin mota cikin girmamawa. Baya ya janye mata kadan,ya saka hannu yana cire cufflinks dinsa a nutse yana ajiyewa saman table. "Ban sanka sani na haqiqa ba" Ta fada a sanyaye,tana tsoron fadawa inda aka girmi matsayinta da Nisan tazarar da zata wafce dukka kimarta "Really?" Ya furta yana dage dukka girarsa gaba daya idanunsa suna rusunawa sosai kaman wanda yasha wani abun maye. Idanunta ta sake zarewa a hankali,da gaske takeso ya dauki abinda take gaya masa. "Kullum saina gano sabon abu game dakai....." Saita dakata. ".....me girma" Ta dora da fadi numfashinta yana sauyawa. Yadda numfashinta ya canza hakan yaji ya tabashi sosai. Ta yaya zai iya jurewa ci gaba da jinyarta ne?,tana juyewa da wani salo da baisanta dashi a baya ba. Sai shima yaja da baya yana jingina da table din dake kusa dashi don ya bashi support. Idanunsa baibar fuskarta ba "And does that scare you?". Ta fahimci wasa da kuma tsokana kawai yakeson maida zancan. Amma gaskiya ne.....kadan kadan abubuwan suna bata tsoro. "......A little" Ta yanke shawarar fadin gaskiyar abinda yake ranta. Wani siririn murmushi ya taba lips dinsa,murmushin fahimtar gaskiyarta da take fada,murmushin fahimtar bata iya boye abinda yake ranta sosai ba. "Na fahimta......zaizo ya wuce,kema zaki fahimci komai...amma" Ya fadi yana dakatawa. "You missed me after only a few hours right?" Idanu ta waro sosai tana sake jin mamakinsa da tsoronsa. "Bance haka ba" Ta fadi da yanayin son karya hasashensa. Can qasa yayi dariya irin wacce ba kasafai yake yinta ba. Idanunsa sun sake rusunawa sosai sanda yake takowa yana dawowa gabanta. "You waited by the window" Ya fada calmly yana sake riqe qugunta da duka hannayensa,kaman wanda ake busawa siririyar sarewa take shiga kunnuwansu a hankali. "You watched for my cars...." Ya sake fada muryarsa tana sakeyin qasa. "......And your heartbeat changed the second I walked in.” ya fadi da muryar rada wadda ta raunata dukkan jinta da gangar jikinta. Kunya.....wata irin kunya ta sake lullubeta "Haisam....." Ta furta da wata kalan kasalalliyar murya. Sai ya sake matseta sosai a jikinsa,yasa yatsansa yana daga habarta a hankali. "Say it" Ya fada cikin rad'a "Me....." Ta fada muryarta tana sake zuqewa itama "That you missed me...." Ya qarasa maganansa ta farko. Da sauri ta girgiza kai,sai ya saki wani kasalallen murmushi......wannan dangerous calm smile din. "Liar" Ya furta a hankali. Zame fuskarta tayi saboda yadda taji dukka jikinta yana amsawa. *zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 08187255862 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 08187255862 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 97* _________________________ https://chat.whatsapp.com/BkfPzSEDhnsIwyCD8LNGkm?s=cl&p=a&mlu=0 *IDAN KINSAN BA ORDER DIN KAYA ZAKI DINGA SAKAWA BA* *IDAN KINSAN BA BUSINESS KIKE DA NIYYAN YI NA KAWO KAYA DAGA CHINA BA KARKI SHIGA* *_DON ALLAH KARKI BATAWA KANKI LOKACI_* *_Assalamu alaikum my loyal people_* *_Barkanmu da wannan lokaci,kuma barkanmu da warhaka_* *_akwai da dama cikin mata wadanda suke sha'awar yin order kaya daga CHINA zuwa NIGERIA,NIJER,CAMERON,CHAD da GHANA_* *_Amma rashin samun amintaccen company....ko hannun wanda zasu dinga siyan kaya ta hannunsu cikin aminci ya hanasu_* *_To a yau addu'ar da yawa daga cikinku ta amsu,don nayo muku tsarabar kamfanin da zakuyi siyayya ta hannunsu su kuma dora muku kayanku har qasarku cikin aminci ba tare da fargaba ko d'ar d'ar ba_* *_kunsan komai nawa TASTED AND TRUSTED ne,to wannan kamfanin idan akwai abinda yafi TASTED AND TRUSTED ma shine_* *_Baki da fargaba kota sisin kwabo,ni SAFIYYA HUGUMA na tabbatar da hakan_* *_Zaki iya kasancewa dasu group nasu,inda a nan zaki hadu da agent dinsu da CEO nasu gaba daya ta wannan link din,zaki samu bayanansu da komai da ya shafi mu'amala dasu_* *INA ME BAKU TABBACIN AMINCI DA INGANCI DA SAUQIN MU'AMALA DASU DA IZININ ALLAH,BAN TALLATA MUKU SU BA SAI DANA GWADA* *Allah ya dafa mana,yasa mana albarka a nemanmu,ya albarkaci halal dinmu ameen summa amee* __________________________ Maganansa ya sanya ta kasa hana qaramin murmushin dake fuskarta fitowa. Sai ta juya zata wuce,still ya kamo yatsuntsa a hankali "Relax mana....." Ya ha fada yana kashe mata idanunsa. "I'm teasing you...."sai ya sakar mata hannun a hankali yana sassauta tie din wuyansa idanunsa a kanta still. " Na gaji" Ta sakejin ya fada sanda shuru ke shirin musu kutse. Daga kai tayi a hankali ta kalleshi. Yadda ya fadi kalmar ne ya sanya ta lura da gajiyar dake boye a muryarsa. "Duk da wannam composure din......ashe ya gaji sosai" Ta furta can qasa ranta. "Sannu" Ta furta kalmar da tarin kulawa cikin sautinta da kuma idanunta,abinda yaji ya masa dadi sosai,musamman sanda ta dora da fadin. "Da alama yau me wahala ce" Idanunsa ya lumshe har kamar bazai bude ba. 'Yar qaramar kulawarta tana nufin abubuwa da dama cikin ranshi dama darensa na yau. Sai kuma ya saki numfashi a hankali yana warware cuff din hannunsa "Meetings.....investors....royal approval......" Ya sake lumshe idanunsa yana dorawa ".....and too many people talking at once....." fada a hankali duk da ba amsar da yayi niyyar bata ba kenan,amma sai yaga ko yaya.....ko yaya ta cancanci taji wani abu koda kadanne da zai kwantar mata da hankali. Maganarsa ta qarshe ta kusa sanyata tuntsurewa da dariua,ta kuma shafe abinda ya kamata ace hankalinta yakai kai. Wato kaman itane.....a duk sanda tayi calling for meeting a sahel couture ba'a cika lokacin ake tashi. Batason hayaniya da dogon magana,amma shi da alama ya fita. Ta murmusa cike da burgewa sannan tace. "Amma ka iya handling komai calmly" Maganan ya qwace daga bakinta,don ba'a zahiri taso furta hakan ba,zuciyarta taso barwa. Idanunsa ya sake dai lumshewar yana budesu dukka a kanta kaman ya qara musu girma yanason ganinta sosai. "Wannan calmness din.....yana disappearing sometimes around you my princess" Bugawa zuciyarta tayi a hankali,ta buga da wani yanayi daya isa har kunnenta ya kuma sanya numfashinta nauyi cikin qirjinta. Suits dinsa na saman ya zare a nutse,kai tsaye kuma ya miqa mata,kamar wanda ya saba yin hakan tunda dadewa. "Zanje nayi wanka na dawo before you start over thinking life again". Rusunawa tayi tana karbar rigar daga hannunsa,wani yanayi daya tilasta masa binta da kallo sanda take juyawa tana wucewa daki da rigar. A hankali idanunsa suka sauka akan qugunta,yadda yake juyawa kaman wanda ke karbar umarni daga wani guri,sai ya samu kansa da miqa hannu kaman zai kamota,sai kuma a hankali ya maida hannun nasa ya dunqule,murmushi yana qwace masa,ya taka a nutse yana bin bayanta. Haka kurum tunaninta yayi nisa sanda takejin motsin saukar ruwa a bathroom din. Me ya kamata tayi?,yace ya gaji. Samun kanta tayi da duba menu dinnan da nanay ta aiko mata a gida a wancan lokacin,ta kammala dubawa tas,sai ta saki qaramin murmushi tana cije lips dinta,ta ajiye wayar tana miqewa,a hankali kuma ta furta "Suruka ta gari". Mintuna kusan arba'in ya dauka,sannan ya fito parlor din sanye da black silk trouser da farar t-shirt me laushi. Sassalkar sumar nan me santsi da ragowar damshi a cikinta. Qamshin fresh oud da sandalwood na biye dashi qafa da qafa. Yau wani qamshi na daban takeji a tare dashi,baqon qamshin da tunda suke sai yau ta fara jinsa a tattare dashi. Sauyin qamshin ne yaja hankalinta. A nutse ta daga kanta daga amsa messages na falaak da takeyi ta zube kallonta a kansa. Ya mata kyau....wani irin sassanyan kyau,ko don bata saba ganinsa cikin qananun kaya haka bane?. Data tuna a gaban wa take kuma saita sauke kanta da sauri. "You're staring" "Ban kalla ba" Ta amsa da sauri,wata tattausar dariya ya sake. "Another lie". Kai ta dauke tana sake jin nauyinsa,yayin da shi kuma ya aza idanunsa akan gurin. Wani irin luxury setup ne.....da warmlight ne a gurin me kwantar da zuciya. " Wow......ma sha Allah" Ya fada yana qarasawa. An ajiye pillows masu laushi qananu qananu wadanda yafi jin dadin zama a cikinsu yaci abinci duk sanda ya gaji irin haka. "Waye ya baki satar amsa?" Ya tambayeta kai tsaye bayan ya zauna yana dubanta murmushi yana qin barin fuskarsa. Yadda taga ya yaba kawai ya sanyata jin wani irin dadi. Take zuciyarta taji tana mararin ci gaba da ganin wannan yabawar.....wannan jin dadin saman fuskarsa. "Komai da komai......ya kamata na koya" Taji zuciyarta tana sake qarfafarta. Tayi qoqarin serving nasa.....zata sake zubawa a wani plate din ya janye,ya saka musu spoon biyu a dukka plate din. "Oya....bismillah" Ya fada yana tattare hannun rigarsa gami da janye nasa spoon din gefe. Bata gasgata da hannu zaici abincin ba sai da taga yayi bismillah yakai abincin bakinsa ya sake wata lomar. "Ya salamm" Ta fada qasan ranta. Komai nashi simple ne?,mutum irinsa amma ya tattare hannu yana cin abinci da hannunsa?. Idanunsa ya aje a kanta yana tauna lomar a hankali,sai daya hadiye sannan yayi magana,komai nasa akwai tsari da ilimi a ciki. Yanason qure rashin cin abincinta a yau,bai taba ganin cin abincinta ba tunda suke. "Eat properly" "I'm eating" Ta amsa masa a hankali. "No" Ya fada da calmness sosai cikin muryarsa. "You’re moving food around the plate dai princess" . Lips dinta ta cije kadan cikin kunya,duk sanda ya kirata princess sai taji ya aza mata nauyi saman kanta. "You noticed too much" Ta furta can qasan maqoshinta. "I noticed only you". Kasa amsa masa tayi,sai wani irin shuru ya gilma,irin shurun dake nuna sabo dakeson kutsowa sosai tsakanin mutum biyun da wata alaqa me girma ta gifta tsakaninsu. Da wani irin yanayi najin nauyi take gyara blanket din,daidai sanda ya miqa hannu ya qarasa kashe fitilar data rage ta gefan gado. Duhu ya mamaye dakin,shuru ya sake gilmawa kafin ta jiyo muryarsa cikin duhun. "Akhnan...." "Uhmmm" Ta amsashi gangar jikinta na kwadayi da fatan samun kusanci dashi,saidai wannan izzar dake cikin jinin kowacce diya mace ya hana ta nuna hakan koda a fuskarta. "I liked today" Ya fadi kansa tsaye da zahirin abinda yake cikin zuciyarsa. ".....coming back to you afterward" Ya qarasa bude mata maganan. Wani irin laushi zuciyarta taji tanayi sanda ta tsinci dumin tattausan jikinsa yana mamaye duk ilahirin jikinta,ya ilahi....batasan sai yaushe zai qyale zuciyarta ta huta ba. Bata sani ba.....qila ko sai sanda ta soma yawo layi layi tana gaya musu haukan son prince haisam aba jifar takeyi?. (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) *NANAY* Cikin qanqani lokaci ta tashi hankalin sassanta dama gidan gaba daya wajen neman inda akhnan ta shiga. Kusan duk wata hadima a tsaye take wajen bincika cikin gidan,maganan yaje har kunnen motii sai gashi da kansa a sassan. "Kina tunanin wani mummunan abu ya isa ya shigo ya shallake kowa yayi gaba da ita?" Motii dake boye dariyarsa ya fada yana duban nanay wadda tashin hankalinta ya bayyana muraran. Kai ta girgiza da sauri. "Nifa ban gamsu ba.....ba inda giiftii zata sanya qafa ta fita ba tare da sanin kowa bafa". Dariyarsa ya sake kalmashewa sosai yana duban qwayar idanunta. Har yanzu duk data girma amma yana iya ganin wannan zallar quruciyartata da yasha fama da ita a shekarun baya saman fuskarta. "Shikenan.....a sake dubawa wataqila a dace ko tayi bacci a wnai gurin" Ya fada yana gyara zamansa kawai. Daidai lokacin rumaisa ke shigowa gurin. Bayanta baiwarta ce obsa,rungume da 'yar magen rumaisa din fara qal wadda ke da wani irin kwantaccen gashi me taushi dake gwada irin kulawar data samu. Idanunta akan nanay,don tun sassafe ta fita makaranta,sai kuma yanzu take shigowa gida. "Lafiya nanay?,me yake faruwa?" Ta tamabaya adan rude ganin yadda kowa yayi carko carko. "Giiftii ce ba'a gani ba rumaisa" Fuska tadan tsuke kadan,da alamun mamaki saman fuskarta. "Ba'a ganta ba?,tunda yaushe?,kunyi breakfast ne tare?" "Aah....tunda sassafe fa?" Dariyarta take qoqari dannewa kadan,sannan ta sassauta fuskarta. "Nifa naga obbo haisam din dazu" Waiwaya nanay tayi sosai tana duban rumaisa. "A ina?" "ta private exists.....kuma kamar giiftii din ce tare dashi,don mun hadu tana fita ina shigowa" Rumaisa ta qarasa fada kamar zata qyalqyale da dariya ganin kallon da nanay take mata dukka idanunta a waje. Data sauke idanunta akan motii kuma sai ta juya fuskarta saboda shima fuskarsa ta nuna dariya yakeson yiwa nanay din "Subhanallahi" Tace a hankali saboda gaba daya ta rasa abun fada. Gurin ya dauki shuru,kafin kuma ta sake cewa komai Aanani dake zaune gefe da wayar nanay din a hannunta tace. "Obbo haisam.....ya turo saqo nanay,kamar ma tun jiya.....kinji abinda yace" Ba tare data jira cewar nanay ba ta fara karantawa a fili. _"Assalamu alaikum_ _Nanay._ _Ki yafe min rashin sanar dake da wuri._ _Na tafi da Akhnan Dubai tare da ni._ _Na san hakan ba shine tsarin da ya_ _dace ba,amma na yi _missing matata fiye da yadda zan iya_ _jurewa._ _I promise tana cikin_ _kulawa da aminci,zan riqe alqawari_ _Ki yi hakuri da ni_ _Nanay_ Wani shuru ya sake wanzuwa a falon,motii ya tattara dukkan jarumtarsa ya cinye dariyarsa yana yiwa rumaisa sign na su fita,sai itama ta baiwa kowa dake gurin umarnin hakan. Sannu a hankali gurin ya zamana ba kowa sai shi da nanay din. Ya sake kallonta sosai yadda ta zama speechless gaba daya. "Kin manta waye d'anki.....haisam baya hayaniya,.....but idan ya yanke abu......yana aikatashi,musamman abinda ya tabbatar yana kan daidai ne,bai kuma sabawa Allah ba" Yayi shuru still yana qoqarin danne dariyarsa kada ta tunzura. "Amma fisabilillahi ya saceta har cikin daki kamar wani qaramin yaro?" Ta fada tana kwabe fuska kamar wadda ta rasa uwa da uba. Dole a wannan karon yabar dariyarsa kadan ta fita. "Ya dauki matarsa ne,ba wata yarinya a waje ba...sannan ma kada ki azawa yarona duka laifin,da qafafunta ta fita itama fa,tabbacin tanaso kenan tabi mijinta,kara kawai take miki" "Ya yaudareta dai.....dama ku maza kun iya yaudara" Ta fada a karon farko tana dan harararsa,irin wasan da suka saba can baya. Murmushi ya sakeyi "Tun farko dama na gaya miki,kada kice zaki tsananta tsakanin lamarin miji da mata....." ".....kaima dai kana goyon bayansa ne dama tun farko" Dariyarsa gaba daya ta subuce masa,royal father laugh dake kama da nutsuwar dake tattare akan fuskarsa. "Dama dariya kakeso kayi ai na lura tun dazu,to kayita dariya" Ta fada tana miqewa. Hannu yasa ya riqota yana fadin "Zo mana.....haba hadeezata" Ya jawota ta koma ta zauna a inda ta tashi. *zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 08187255862 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 08187255862 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 98* *DU B A I* Lallausar safiyar da wani siririn haske da iska me dadi ke kadawa sosai tsakanin kowacce qofa da window na penthouse din nasu dake cikin Atlantis the royal. Saman tsararren dining din dake shiyya ta musamman cikin residence din,dining din da aka cika da kalolin breakfast iri iri,tamkar mutane da yawa ne zasuci,bawai iya khadeeja da muhammad ba. Yarima haisam ne zaune kan kujerar dake opposite na akhnan Sanye yake da pure white Tom Ford shirt da charcoal trouser,hadin color din daya fidda wani launi me kyau,irin launin da zai gaya maka ansan ainihin hada colors su bada ma'ana me kyau. Hannunsa sanye yake da black Patek Philippe watch wanda ya kwanta saman kyakkyawar fatarsa da gargasa ta yiwa ado me daukan idanu. Sanda yake fitowa,idanunta sun sauka akan berluti shoes din dake qafarsa,wanda yake bayyana asalin tsada da dukiya,saidai bada murya me amo ba,don zaka dauka gama garin takalmi ne,amma kuna sananne ne a idanun wadanda ke rayuwa daidai ko kusa da mizanin nasa arziqin. A nutse yake sipping coffee din nasa,yana qare mata kallo cikin wata doguwar riga midnight blue data haskata kamar zaka saceta ka gudu. Shi ya zabi rigar da safiyar nan,yace ita yake buqatar gani a jikinta,zai kuma zabi shigar da zata masa da dare idan ya dawo. Bata iya zama haka ba,sai data dora qaramin farin baby hijab daya nuna fuskarta a tsakiya da wani irin kyau da kwarjini. Ya sani,ta masa rowa,don ta rufe abinda yake matuqar mararin kalla wato albarkatun qirjinta A zahiri suna zaune ne cikin shuru,saidai a badini wata hira ce akeyi tsakanin idanuwa da zukata,wannan karon baki baida rawar takawa ko abun fada. Karo na hudu ya sake sauke idanunsa akan qirjinta daya ciko fam ta rigar,amma ta hanashi ganin komai banda wannan tudun. Kasa jurewa yayi,ya miqa hannunsa a hankali dake daure da agogon,yasa yatsunsa don hanye inda hijab din ya rufe. Da sauri ta riqe hannunsa caraf zuciyarta tana bugawa. Har yanzu ta kasa goge abinda ya faru daren jiya,bai mata komai ba.....amma ya fidda dukka maitarsa da soyayyarsa da gurin,har yanzu kuma tana jin kowanne feelings a jikinta. "No" Ya fada can qasan maqoshinsa yana sarqe idanunta cikin nasa. "It's my halal,karki hanani kalla.....kinaso idan na fita na kalla na wasu a waje?" Ya fada yana langabar da wuyansa kamar marayan dake neman tallafi. A hankali ta sakar masa hannun,NA WASU A WAJE daya fada sai taji kamar ya dauki mashi ya caka mata a qahon zuciyarta......sai taji zuciyarta tana mata nauyi da wani irin kishi. Idanunta suka dan sauya kadan tana kallonsa. Kamar yanzu ne ta fara fahimtar cewa......Haisam mutum ne da mata zasu kalla. kuma duniya cike take da irin kallon da take masa yanzu. "Kada ka qara fada.....don Allah....banaso". Wani irin abu me sanyi yaji yana ratsa dukka jikinsa. "Kishi.....kishi na take?" Ya fadawa kansa da kansa. Wannan dabi'artata ta masa,bata iya boyen komai,muddin dai ta daukeshi da muhimmanci. Hannunsa ya miqe a nutse ya kamo yatsunta cikin tashi ya saka a nasa hannun yana murzawa softly. Kai ta dauke taqi kallonsa,ya sake sakin murmushi dan kadan "Hey..." Ya furta softly yanason sake ganin wadannan blue eyes din. "I was joking" Ya fada a nutse. Kallonsa tayi saita sake kauda idanunta. Da gaske taji zafi,wani irin zafi da batasan zuciya na iya jinsa ba,kuma har yanzu zafin takeji "Ni banason jin kana kallon wata" Ta motsa labbanta a hankali ta fada kamar zuciyarta tana karyewa. Wani soft smile ne ya bayyana saman labbansa,not mocking.....fond.....very fond. "My princess....." Ya kirata da wannan sautin dake kasheta. "“I barely look away from you.”. Idanunta ta lumshe saboda yadda muryarsa tayi taushi da yawa. Yadda ta lumshe idanun sai ya hade eyelashes dinta na sama dana qasa,saita sake masa wani irin kyau me daukan hankali. Gaza jurewa yayi,yakai hannunsa ya shafi gefan fuskarta. "There’s nothing outside more interesting than my wife.” ya motsa labbansa a nutse yana hada kalmomin. Ya rasa da wanne sabulu take amfani,baisan da wanne abu take kula da fatarta har haka ba......amma yanasan ran wataran zai gani.....zai kuma tambaya. Da dukkan wata kalma daga bakinsa sai da zuciyarta ta buga.....wannan karon ba saboda kishi ba.....aah.....saboda shi. Saboda shi dai....wannan malamin.....saboda shi....wannan yariman.....saboda shi....wannan boyayyen identity din da take xuba idanu taga ranar da zai gaya mata komai da bakinsa. "Kaine mutumin hippodrome?" Tambayar ta subuce mata sanda yake maida cufflinks dinsa. A bazata maganar tazo masa,amma sai ya daga kansa da murmushi yana dakatawa daga sanya cufflinks din. Da wannan dangerous smile din nasa yake takowa inda take zaune,hannayensa zube a aljihun wandonsa da ya yiwa tucking. Ya lura wannan tambayar na daya daga cikin manyan tambayoyin dake damunta. Sunkuyawa yayi daidai fuskarta,ya bata lite kiss kaman yadda ya saba,sannan a nutse yace. "Nayi alqawari.....zan baki amsarki.....not now,idan na dawo". Ta gamsu da maganansa,kuma yadda ya amsa matan sai ya qara zumudinta nason jin amsar tasa. "Da shehnaz da aisa.....zasu iso dubai yau in sha Allah,nan da hour biyu.......zasuje bikin bude wancan kamfanin dana gaya maka,dukkanmu fan na brand dinne" Tayi maganan qwayar idanunta bata kallon nasa. Murmushin gefen baki yayi,a nutse ya dakata daga takawar da yakeyi. "Ma sha Allah....dubai na musu barka da zuwa" Yadda yayi maganan kamar dubai mallakinsa ce ta sanya ta daga kanta tana dubansa,sai ya basar yana jawo briefcase dinsa. "Zanje tarbosu......don Allah.....zasu sauka a five falm Jumeirah". Shuru ya danyi sanda yake bude briefcase din nasa. Ta lumshe idanu tana dan jin fargaba. Idan ya hanata zuwa tarbarsu.....kenan hakan yana nufin yawon da zasu d'an fita susha iska ma bazai bari ba. "Karsu sauka a Jumeirah......zan saka a bude musu dayan suite din dake cikin residence din nan su sauka a ciki" Jerarrun fararen haqoranta ne suka fito,wadanda suka qara mata wani irin kyau. Tsaiwa yayi cak yana kallonta gami da jin komai yana tsaya masa da murmushinta kawai. "Na gode.....na gode sosai" Idanunsa ya lumshe yana budewa,sai kawai ya bude mata dukka tafukan hannayensa. Batayi tunani na biyu ba,ta miqe a hankali,tana takawa kamar me tausayin qasa,yanayin takunta da yake sanyawa wani lokaci yake kishinta idan tana tafiya a waje....saboda yana ganin kamar kowa idanunsa yana kanta. A nutse ta fada faffadan qirjinsa tana sauke ajiyar zuciya......shi kuma ya maida hannuwansa ya kulleta a ciki yana matseta a tausashe. Ko sau dubu jikinsu zai hadu.....sau dubu idan zai sake rungumeta yana jin kamar yau ne.....yanzun ne runguma ta farko a rayuwarsa da zaiyi mata. "......sannan" Ta fada a hankali tana fargabar gaya masa,amma husky voice dinsa data cika mata kunne ta bata qwarin gwiwa. "Fadi kawai.....aminci ne tsakaninki da mijinki......ba tsoro ba" "Zamu fita......sunason small outing.....na kwana biyu ko uku" Shuru ya ratsa tsakaninsu,sai bugun zuciyar junansu dake ratsa kunnuwansu. Na wasu mintuna,ya zane jikinsa a hankali,sai itama taja baya tana sauke idanunta a kansa. "Shikenan.....bazai bari ba,dama aisa ta fada i wasn't like i was before,ina da aure yanzun" Ta fada a hankali idanunta yana son tara hawaye ganin baice komai ba yana komawa cikin daki. Jikinta a sanyaye ta koma saman sofa tana zama,tuna zurfafa tunaninta. "Take the security team" Taji soft voice dinsa a gefanta yana furtawa a hankali sanda yake zama a sofa din dake dab da tata yana maida socks din qafarsa. Idanunta da suka cicciko da qwalla ta daga tana dubansa,sai shima ya nutsa nasa qwayar idanun sosai cikin tata sanda yake maida safar cikin lallausar qafarsa. "Da gaske?" Ta fada da wani irin ban mamaki. Murmushi ya sakar mata ne laushi wanda ya narka wani abu me sanyi cikin zuciyarta. "Did you expect me to say no?” ya tambayeta yana dage mata girarsa gaba daya bayan ya kammala maida socks din yana soke yatsunsa duka cikin na juna. Kunya ta kamata na yadda ta yanke hukunci haka kai tsaye,sai ta danyi qasa da kanta. Ya saki siririn murmushi yana janye idonsa daga kanta. Wallet dinsa dake gefe ya dauko ya bude. Wani black card ya ciro,da wani car key,sai wani katin na daban ya dorasu saman table din dake tsakaninsu. "Use this" Ya fadi a taqaice,maganan data sanyata daga kai tana duban inda ya ajiye kayan. Sanda ta saka hannu ta dauka sai taji komai yana mata sanyi. Keys ne na motoci kusan kala biyar,black card wanda base an gaya mata darajarsa da kuma a hannun waye ake samunsa ba.....sai wannan card din data gaza gane ne meye. "Haisam" Ta fada a sanyaye. "Oh my god" Ya furta softly. Baisan meye a muryarta haka ba,da idan ta kirashi komai yake kwancewa daga cikin kansa ba. In zata maimaita sunanshi sau dubu yanaso,bazai gaji daji ba,har baya fatan wataran ta sauya sunansa da wani sunan na daban. "Wannan fa?" Ta fada tana dan jin nauyin tambayar,amma kallo daya ya masa ya amsa mata kaman bai fahimci nauyin abinda takeji ba. "It gives you access....." Yadan dakata. "........to restaurants.....lounges.....shopping floors" Sake tsayawa yayi kadan. "........dama duk inda kikeson zuwa" Sake bude wallet din nasa yayi,sai ya ciro wani slim metallic card yana sake ajiye mata. ".....And this one is for restricted places.” "Restricted?" Ta fada can qasan zuciyarta lamarin yana fara girmamar kanta. "Yeah.....So they stop asking questions the second they see you.” kasa magana tayi,har sanda ya sake takowa gabanta,ya kama hannunta yayi kissing deeply. " Ki kulamin da kanki.....sannan 2days yayi yawa kina fita.....if possible zan sadaukar musu da kwana biyu.....kwana dayan nawa ne.....zamu huta saboda next day kinaso kije kiga grand opening right?" Kamar wadda kanta ya karye haka ta gyada masa kai a hankali. Ya lumshe idanunsa yana sake budesu dukka a kanta,yanason ta tashi ta rungumeshi so samu,ta bashi deep kiss,amna bayaso ya cika matsa mata,don haka yayi waving mata hannayensa yana fita da baya da baya har ya kammala fita gaba daya. Da taimakon ambaton Allah yanayinta ya daidaita. Ta zauna kawai tana juya duka cards din daya bata. Batasan wanne kalar tunani zata sakeyi kuma a kansa ba,kawai maganan jiya ne da zuciyarta ta gaya mata. Ta samawa kanta salama,ta kalli komai kawai.....ta jira sanda ya shirya fito mata a mutum. Aiki suke da agogo ko aiki da lura ko zallar sanin makamar aiki ne bata sani ba. Amma abinda yafi bata mamaki sanda security alert ya gaya mata security team din suna jiranta don rakata airport dauko su shehnaz. Haka kawai ta samu kanta kalar shigar data lura idanunsa sunfiso,shigar da zata rufe komai nata banda zagayen fuskarta da tafin hannunta. Yalwatacciyar abayar da asalin matan sarakuna a qasar dubai ke amfani da ita,sakakkiya sosai wadda ba abinda zata nuna nata. Daga bakin residence dinsu ta fara cin karo da security uku. Abun mamakin dukka mata ne,su suka karbi jakarta suka riqe mata suna gaidata cikin girmamawa,sannan suka shiga private elevator din suna sauka qasa.💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 99* Mota hudu ne,kowanne akwai security a ciki. Qwaya daya ce kawai maza amma duka sauran mata ne a ciki. Tafiyar mintuna kadan suka isa dubai International Airport,kuma suka samu tuni jirginsu shehnaz ya sauka,don duk duka batafi jiran minti sha biyar tayi ba taji ana kiran sunanta. Ko bata waiwaya ba tasan shehnaz ce,wani tattausan murmushi ya subuce mata sanda take juyawa. Sanda idanunsa suka hadu itama saita gaza jiran qarasowarsu,ta fara takawa don isa garesu,da sauri daya daga cikin security din tayi mata magana "Easy ma'am.....please allow us to secure the area first". Tsaiwa tayi tana sake tattara nutsuwarta,kaman yadda shehnaz ta dakata cak tana bude idanunta cikin mamaki. " Ba zaki qarasa gurinta ba sai an tabbatar da ingancinki" Aisa ta radawa shehnaz tana qyalqyalewa shehnaz din da dariya. Clearing hanyar suke mata da gaske,cikin wani strict professionalism.....kamar tana qarqashin important protection da dukkaninsu idanuwansu suka gani. "Ku daina kallona haka mana" Akhnan ta fada sanda suke takawa qarqashin kulawar security zuwa inda motocinsu suke suna damqe da hannun juna dukka su ukun "Wallahi sai yanzu nakejin kamar kina wata different duniya da tamu" Maganan ya saka akhnan sakin dariya kadan,mai hali baya fasa halinsa,ba abinda xai sauya shehnaz dai da gaske. Ko a cikin motar bakinsu dukka yaqi mutuwa,kada ma shehnaz taji labari. Ba abinda ta rage daga abinda idanunta suke gane mata. "Wacce empire din ya kaiki ne akhnan?" Shehnaz ta fada tana kama bakinta idanunta cikin na akhnan. "Shehnaz manaaaa" Ta fadi da irin salon yadda take magana idan shehnaz din ta dameta a baya da dogon surutunta. Murmushi aisa tayi,sannan tace. "Na baki shawara?....ki qyaleta kawai,duk abinda yake cikinta saita fada,gwara ki rabu da ita" Cikin girmamawa da sanin aikinsu daya daga cikin security din data fuskanci itace shugaba take tambayarta,zasu ci gaba da tsaiwa suna jiranta ne?,kamar ance zata sake fita,ta amsa musu kafin ta juya suna shigewa ciki,kunnuwanta suna cika da maganganun shehnaz. "Tun a elevator.....ba button na floors.....sai access card kawai.....private royal suit guda.....ni da aisa kawai?....biftu....wannan ba hotel bane.....Masarauta ce" Ta qarasa fada tana fadawa saman lallausan gadon dake da girma da fadi bayan da akhnan ta nunawa aisa nata dakin daban. Dauke idonta akhnan tayi daga kan shehnaz tana maidawa kan aisa "Don Allah har yanxu jamaal baice komai ba?......na gaji da wannan bakin inaso a kullemin shi" Batasan magananta ta bada wata ma'ana ta daban ba,sai da taji sun sake mata shewa su biyun. Hannuwanta ta daga musu. "Don Allah,kada ku fassarani". Hutawa sukayi sosai,cikin mintina aka wadatasu da dukkan abinda suke da buqata. Ba shehnaz kawai ba,aisa da kanta daga qarshe kasa shuru tayi itama. Awa daya kawai dukkaninsu suka shirya suka fito,suka samu security team din suna jiransu kamar yadda suka umarta. Basu aisa kawai ba.....hatta da akhnan kanta ya sake kwanceta fitar da sukayi. Guraren da suke kashe kudade masu yawa.....guraren da suke kula da shigarsu a yau sun shiga sun fito ba tare da sunsan sun kashe komai ba. Batasan girma da kimar da yake dasu haka ba cikin qasar.....wanda iya card dinta kawai ake kalla a duk inda sukaje din sai taga an ninka girmamawar da ake bata. luxury malls.....rooftop lounges......waterfront restaurants......designer stores.....amma duk inda suka shiga da zarar Akhnan ta nuna card din. Staffs nasu suna sauya attitude instantly.....still kuma ana kaisu VIP sections a kowanne guri da zasuje din. Daidai da boutique din da sukaje private collection room aka kaisu. "Wow" Kawai shehnaz ta fada. Kaman yau ta fara sani ko ganin luxury,sai takejin kanta yana sake girma da fadi. "Sheikh dinnan....wannan sheikh din naki ya wuce duk zatonmu.....me yasa ya boye kansa haka?,anya ba yana sane bane kuwa?,anya ba wani babban dalili kuwa?" Shehnaz ta fada tana fidda idanunta waje sosai. "Kudi ne da mutumin nan irin na films" "......ba kudi kawai ba shehnaz....influence" Aisa ta fadi itama abun yana tsumata. Tambayar qarshe da suka mata bayan sun koma gida. Shehnaz ta rutsata. "Don Allah biftu mana.....wannan fa ba sheikh dinnan bane na agadez.....ki gaya mana waye haisam?" Tana daure zaren igiyar rigar baccinta ne sanda shehnaz take mata tambayar,kanta cunkushe da tunani,saita samu saman sofa bed ta zauna tana dubansu da blue eyes dinta. "Mijina" Ta furta kai tsaye don bata da amsar data wuce wannan. "Akhnan" Aisa ta fadi tana sake samu tabbacin wani abu game da abinda yake faruwa yanzun haka a sahel couture. ".....barta mana aisa.....bafa wannan muka tambaya ba" Ta fada tana fiddowa akhnan ido waje,abinda ya tilastawa akhnan din murmusawa. Idan wannan tambayar ce....itama har yanzu neman cikakkiyar amsarta takeyi "Kinga yadda mutane suke rusuna masa kuwa?" Aisa ta fada fuskarta dauke da tarin tambayoyi da kuma murmushi. "Ke bakiga yadda ake sauya komai saboda sunansa kawai ba?" Shehnaz ta fada tana rungume da hannayenta. Komai burgeta yake.....amma mamakin da suke shiga yafi qarfin kwatance. "Ni kaina ban gama fahimtar hakan ba....ni kaina a rude nake har yanzu" Ta fadawa kanta da kanta ba tare data bari sunji ba. Security alert na qofar suite dinne ya kada,alamun akwai wani kusa da qofar. Hirarsu ta katse da tarin tambayoyinsu,suka maida dubansu ga akhnan. "Bari na duba" Ta fada softly tana miqewa gami da zura flip flops dinta. "Dawo ki dauki wayarki,don idan mijinki ne babu lallai ya barki ki dawo" Aisa ta fada tana dariya shehnaz tana tayata. Tsaiwa tayi cak,sannan ta waiwayo tana watsa musu harara. "Banason sharri.....be dawo bama ballantana kuce shi dinne". " Zamu gani.....idanuwan sheikh na rantse da Allah cike suke da giyar qaunarki....kowanne motsinki akan idanun security dinki,wanda na tabbatar suna aikinsu ne da qaqqarfan gargadinsa na su kula dake". Bata waiwayowa ba ta biyewa zancan shehnaz,saidai har cikin ranta tana jin saukar kalamanta,ta kuma ga hakan itama,ta yarda dari bisa dari,amma idan tace zaya biyewa shehnaz ne to zasu kwana suna musu. A hankali ta murda qofar tana budeta. Zuciya daya.....ruhi daya dake rayuwa cikin gangar jiki guda daya suka bayyanawa juna. Yarima haisam ne......sanye cikin dark gray din silk pajamas masu gajeran hannu da dogon wando. Sassnyar iskar dake yawo cikin Atlantis the royal tana kada daddadan turaren nasa kamar yadda take kada sassalkar sumarsa dake kwance saman kansa. Da alama ya dawo tun dazun,kuma har yayi wanka sannan ya sauya kayanshi ba tare data sani ba. Ta qifta idanunta har sau biyu a kansa saboda yadda ya mata wani irin sassanyan kyau cikin hasken fitilun alfarma da suka qawata ginin gaba daya. Baiko barta tayi tunani na biyu ba,ya saka hannunsa dukka biyun ya dagata cak kamar ya samu baby doll,ya rungumeta sosai cikin qirjinsa sannan ya juya ba tare daya damu da rufe qofar suite din ba. "Ka saukeni please,zan iya tafiya da qafafuna" "No need.......indai ina tare dake ba buqatar sai qafafunki suna aiki,tawa ta ishemu" Ta motsa zata sake magana,sai bai bata wannan damar ba,ya hade bakinsu guri daya yana takawa da ita sannu a hankali har suka isa suite din nasu. Ta dauka zai sauketa ne ta taka da qafafunta tunda sun shiga ciki....amma akasin hakan ci gaba yayi da tafiya da ita,bai kuma sauketa a ko ina ba sai cikin bedroom din da a yanzun suke sharing shi da ita. Ya kulle duka sauran bedroom din guda biyu ya hana mata maqullin. Saman lallausan gadon ya direta sannan yayi mata rumfa. Da wani irin zafi zafi yake aike mata da saqo.....wasu irin saqonni da suka soma bin jininta cikin mintuna qalilan. A yau....bar mata bakinta yayi a bude,baiyi yunqurin komai na rufe mata shi ba,saidai da kanta.....a karan kanta ta kasa kiran sunan kowa.....ta kuma kasa tabuka komai saboda yadda saqon ke shigarta da wani irin tasiri me gigita tunani. Sai daya kaita wata duniya me nisan gaske.....sai daya kaita qololuwa sannan ya zame jikinsa a hankali yana sauke wani irin numfashi. Shuru ne ya ratsa tsakaninsu,wani irin shuruuuu daya shige har cikin kawunansu. Ya runtse idanunsa sosai yana riqe tsintsiyar hannunta da wani irin qarfi da sai da taji riqon har cikin qashinta,a kasalance ta furta. "Wayyo Allah" Mirginawa yayi yana maidata cikin jikinsa da kyau yana matseta sosai wannan karan har sai data saki qarar me dan qarfi. "I'm sorry....." Ya fada dukka jikinsa yana rawa. "Me yasa zaki tafi ki barni?......me yasa zaki barni a kango?,me yasa zaki sanya na dauki alqawarin da zai wahalar dani?" Ya fadi yana kamo fuskarta ya hade da tasa yana sauke wani irin wahalallen numfashi,gumin da yake tsatsafowa daga kowanne sashe na jikinsa yana ratsa fatarta wadda tuni ya kauda komai da zai zame masa shamaki daga nutsewar fatarta cikin nasa. "I'm sorry......kayi haquri" Ta fada softly tana motsa labbanta da wani yanayi daya tilasta masa kama lips din nata ya tsotsa da kyau. A hankali ya zame bakin nasa daga nata,ya sake riqe fuskarta sosai a tausashe "Ke tawa ce......ni kadai giiftii.....ba zanyi sharing dinki da kowa ba" Ya fada yana zamewa daga jikinta. A karo na biyu ya sake saka hannu ya dauketa cak,ba tare daya damu daba komai a jikinta ba,ya kuma wuce kai tsaye da ita zuwa bathroom,tana qanqameshi saboda nauyin hakan da takeji,saidai batasan hakan da takeyi sake kunnoshi kawai tayi ba.💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 100* *_THE REVEALS_* Wani shiryayye kuma lafiyayyen grand opening ne da labarin yinsa ya zagaya duniya gaba daya. Wani bikin bude kamfani da yasha banban da saura......bikin daya tara manya manyan shuwagabannin larabawa masu yawan gaske. Al'umma daga kowanne sassa na duniya.....bikin kuma da aka shirya gabatar dashi da daddare sab'anin rana. Da wannan amintaccen hasken na qasar dubai,wanda ya zame mata kamar wani ado daya sake banbantanta da kowacce qasa a duniya. Kamar duk duniya sunfi kowa sanin martabar haske da qyale qyale na rayuwa. Qarfe bakwai na daren.....sanda wasu irin golden light suke walqiya cikin babban dakin taron sabo dal dake wata shiyya daban na kamfanin. Manyan glass windows da na building din gaba daya an qawatashi da wasu irin fitilu gold color.....flowers masu tsada cakude da daddadan qamshin turare mafi tsada da girman daraja daga gurin larabawa wato oud. Tako ina qamshin sa ne me dadi yake tashi,qamshin da zai gaya maka da gaske bikin bude kamfanin turare ne. Daga gefansa take zaune....cikin Rolls Royce din da a yau da kansa yake driving dinta ba tare daya buqaci driver ba. Wani irin kyau yayi mata,wani irin kyau dake fusgar idanu da hankulan kowanne mutum. Kanta ta dauke a nutse tana maidowa kansa. Ya jima a waje yana gaya mata gashinan dawowa.....ya jima da fita yana gaya mata zaizo da kansa ya kaita,har ta fidda rai,tana kuma kallo su shehnaz da aisa sukabi su maleek da falaak da suma sukace mata sunzo ganin bikinne. Ta danyi mamaki,idan shehnaz da aisa fan din brand dinne.....batasan maleek da falaak a wannan harkar ba. Tanata juya wayarta tana kallon yadda lokaci yaketa gudu,idanunta sunata tara hawaye tana hanasu xubowa sanda ya shigo. Wayace a kunnensa yaketa amsawa,yayi cak yana zuba mata idanu kafin ya ware mata hannuwansa,ta taso kaman hakan take jira ta fada ya rufeta a qirjinsa. Still bai daina amsa wayar ba wadda da larabci yake duk maganan da yake,wannan ya sanya bata iya gane abinda yake fada. Wayar dai bata qare ba,don yana ajiyewa wani kiran zai shigo,a haka ya taimaka mata ta fara shirya kanta cikin wata baqar laffaya da aka yiwa adon gold stones. Sai daya taimaka mata ta gama nade jikinta tsaf sannan ya saki wayar tayi gefe. "Ya salammmm.....zan iya?" Ya fada yana motsa maqoshinsa a hankali. Idanu ta fidda waje tana dubansa,gabanta yana faduwa,kada dai yace an fasa zuwa....indai hakane batasan wanne irin kuka zatayi ba "Ina kishinki.....na rantse da Allah,inajin kamar kishinki zai iya kasheni......" Ya fada idanunsa suna lumshewa can qasa da wani irin emotion cakude da kishi. ".....idan wani ya kalleki biftu.....koda sau daya ne......inajin kamar na shafeshi yabar duniya.....inajin kamar kowanne namiji yabar duniyar nan.....ya barmin duniyata dake kawai a ciki" Ya qarasa fada yana mata wani kyakkyawan riqo cikin jikinsa kamar zai hadiyeta. Saidai taji nasa kishin baikai nata ba.....nasa kishin kaman salam ne akan nata sanda ya fito cikin shigar wata irin suite da hannunta bai taba kaiwa kan fabric irin nata ba. Har ji tayi kaman bata iya shaqar numfashinta da kyau,duk yadda takeso suje gurin,sai taji kamar tace masa su fasa. "Yadai?" Ya fada sanda yaga yanayin fuskarta yana sauyawa. Kanta ta kwantar a hankali hannun kujerar. "Zasu kalleka......." "......dukkansu maza ne.....maza suke komawa a idanuna......wallahil azeem biftu" Ya fada yana kama tafin hannunta yana murzawa a hankali. "Mu tafi?" Ya fadi bayan ya dauke idanunsa daketa haske. Kirane yaketa shigowa ba qaqqautawa wani yana bin wani. "Muje....kiranka akeyi" Ta fada tana sauke idanunta akan wayar da taqi daina haske. "Zan iya dakatar da komai saboda ke.....har sai kin amince kin gamsu mu tafi din" Ya fada yana daukar wayar. Cikin idanunta yaga kaman tana suspecting wani abu.....don haka ya haska mata fuskar wayar da sunan OMAR keta yawo akan screen din. "Bayajin magana.....tunda suka hadu su shidan.....zasu cinye miki ni" Ya fada yana langwabe mata kaman yadda ya saba. Taji kunya ta kamata,ta saka hanny ta rufe fuskarta. Ta sani ya fahimci abinda yake mata yawo cikin rai,shi yasa ya goge mata wannan shakkar ta hanyar nuna mata me kiran. "Indai ina kusa.....bazan dagawa kowa qafa a kanka ba". "Ya ilaheeee..... Maimaita don Allah" Ya fada kamar muryar wanda yasha giya ya bugu. Cak ya tsaida komai,wannan kalmar kawai ta hanashi tada motar har sai data maimaita don kada su makara "Da gaske nake....zan fito na fito da duk wada keda shirin matsa ma zaman lafiyarka" "Oh my goodness!!" Ya fada yana riqe tafin hannunta cikin fuskarsa. Ko yanzun da suke gaban building din,tana ankare da yadda security suka zagaye motar. Shi kuma ya zuba mata idanu. Hannunta ya sake riqewa sosai yana murzawa a hankali,yana jin santsin fatarta da laushinta suna ratsashi. "Anya zan iya?" Ya fadi ba tare da yasan maganan ta fito a fili ba. Kallonsa tayi,kallon dake alamta masa taji,sai ya sauke wani numfashi me nauyi yana sake kwantar da kansa saman tafin hannunta. "Kimin alqawari don Allah.....inajin kamar na hanaki shiga.....amma bazan iya ba" Idanunta ta lumshe,a yadda ta kwadaitu da son shiga gurin,ba zataji dadi ba.....amma idan hakan ya yanke,zata jure. "Fadi" "Ba zaki kalli kowa ba" "Zan zama makauniya na awanni duk don saboda kai" Baisan sanda ya raba shingen dake tsakaninsu ba.....ya mata wata kyakkyawar runguma ta mintuna "Allah yayi miki albarka" Ya fada yana sakinta a hankali. Daga jiya zuwa yau kawai sake rikita masa lissafi takeyi,nan gaba idan ya gama horonsa yana hangota a matsayi best romantic wife. Da kansa ya zagaya ya bude mata,ta sanyo qafafunta waje. Ga mamakinta duk security din sun watse,batasan kuma me ya watsasu ba. Tanata ganin tahowar wasu mutane masu baqaqen kaya amma sai taga sun waske basu qaraso gurinsu ba,ko sun koma da baya,bata fahimci komai ba suka fara wucewa ciki,inda ta fahimci an fara gudanar da taron. "Wannan opening din yana da girma sosai" Ta fada a hankali gurin yana qayatar da ita. "Uhmm" Kawai ya fada a hankali da yanayinsa da taga yana komawa wani boss sosai a idanunta,kwarjinin nan da kamalarsa sai taga tana sake hauhawa. Sake kallon giant black backdrop din hall din tayi. Sai idanunta suka tsaya cak. *MAISON AKHNAN* sunan ya bayyana baro baro. Idanunta tadan lumshe a nutse "Akhnan?" Ta maimaita sunan kamar ba nata ba,saita waiwaya tana kallonsa. Ido suka hada,dan siririn murmushi na gefan baki yayi sannan yaci gaba da takawa hannunta cikin nasa. "Irin sunana?" Ta sake fada a fili saboda gaza boye mamakinta da tayi. "Does it?". Bata amsa masa ba,sai tunaninta ya cilla kawai coincidence ne.....ko wani family name ne....ko branding style kawai. Shigowarsu hall din ya danyi shuru.....Mc din dake magana yadan dakata kadan,kamar kuma wanda aka bawa umarni sai kawai yaci gaba da maganan da yakeyi. Cikin shakka da kokwanto taga suna nufar VIP section na baqi bisa jagorancin wani security guda daya dake sanye da baqaqen kaya idanunsa toshe da baqin glass. Har suka zauna bai saki hannunta ba,kamar yasan hakan ya taimaka mata qwarai wajen iya takawa har zuwa mazaunin data cika da mamakin wanne iko ne dasu da zasu zauna a nan?. Abu na biyu idanun da ta gani a kansu ba zata iya qirgasu ba......su suka sake daburtata....girma da tsaruwar gurin.....uwa uba yadda dukka hankula suke sake daukuwa a kansu tun bayan shigowarsu,sai takejin kamar wannan shine karon farko data fara shiga taro irin wannan. Daga gefansu kadan ta hangi su shehnaz......Anaani....rumaisa....balqess harda hansaaa. Daga can bangaren kuma su khadeem dasu amjad,saidai sunfi kusa da haisam akan inda take zaune din. Ta sake jin mamaki yana saukar mata. Dukkaninsu a VIP?. Wata nutsuwa ta ziyarci gurin,kamar an musu wahayi,a hankali me gabatarwa ya sake bayyana da magana cikin nutsatsen turancinsa. "Tonight, we are not merely celebrating a fragrance company…” babban screen ya haska daga bayansa. Bottle design na turarukan masu matuqar kyau suka soma bayyana. Cak akhnan ta tsaya tana tattara hankalinta akan bottle din. Wadannan turarukan data sansu.....tasha amfani dasu,bayan wasu lokuta kuma sukayita bacewa daga kasuwa daya bayan daya. Canzawa screen din yaci gaba dayi yana nuna mayan turarukan da duniya ke magana a kansu,wanda dukkaninsu daga ainihin brand dinta ne na amana.....company din da tafiso,turarukan da sukafi kowanne karbuwa a duniya,luxury collection din da ko ina ake magana a kansu,guraren iko sarauta da manyan attajirai. "Wadannan brands din....." Ta waiwaya cikin magana rad'a rad'a tana gaya masa,sai kuma ta dakata saboda yanayin fuskarsa da taga ya sauya. Ya zama wani cikakken boss. Wannan kwarjinin yana sake mamaye fuskarsa. Wannan din sheikh muhammad haisam take gani. Idanunsa akan stage ya amsa mata. "Yes" Ba tare daya waiwayo ba. Kafin ta sake cewa komai muryar host din ya sake cika dakin taron. 💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 101* ________________________ *_Amintaccen gurin siyayya_* *_ingantattun kaya akan ingantaccen farashin da ba irinsa a kasuwa_* *_BONONZA DA PROMO akai akai_* *dukka sai a HUGUMA CLOSET* *Duniyar kayan yara,mata,maza,dukka* *shaddodi,atamfofi,laces,abayas,jakankuna,takalma,agogo,sarqoqi,English wears,night wears,under wears,da duk wani nau'in sutura babba da qarami* *_Karki yadda ayi babu ke.....leqa kiga yadda closet din HUGUMA kullum ke cike da kaya akan farashi me kama da KYAUTA_* *_YAN SARI....YAN REPOSTING.....DA SARAKAN ADO MASU SIYA DON KANSU....DUKKA INA MUKU MARABA_*🤝🤝🤝🤝 https://chat.whatsapp.com/FrqgC0YmUWP4FPmUzYuLJX __________________________ "The man behind one of the most exclusive fragrance empires in the Middle East…” sai ya dakata sauran maganan yana amsa kuwwa cikin dakin taron. "......the founder of Maison akhnan" Sunanta ya sake amsa kuwwa cikin dakin abinda ya sanya gabanta bugawa. "PRINCE HAISAM MOTII ABA JIFAR". Gaba daya hall din ya karade da tafi da sowa da yabo,abubuwan da suka cakude gaba daya suka cushe kwanya da tunanin akhnan na wucin gadi,suka kuma dagula duk wani lissafi da take zaton tana dashi. Sunan da host din ya kira ke sake amsa kuwwa cikin kanta,ta waiwaya a hankali sanda take hangoshi.....sanda Business elites suke miqewa cikin girmamawa,sanda tarin cameras ke juyawa kansa. "Bayason camera a kaina....wannan dalilin ya sanya ya dan banbanta gurin zamana da nasa?.....inde haka ne da gaske shine....." Kasa qarasawa tayi saboda wani abu da taji yana sauka saman zuciyarta a hankali. Tana kallonsa sanda ya miqe,Kamar wanda wannan ikon ba sabon abu bane gare shi. Wani irin pure power without noise a tare dashi. Dole ta gabanta zai wuce,tana kallon yadda ya rage wannan ginshirar tasa sanda ya iso gabanta,ya rusuna kadan. "You looked surprise?" Ya tambaya cikin salon tsokana,saidai ita a wannan matakin,ba tsokanar takeji cikin kanta ba,wani abu daban takeji daya girmi tsokanarsa. "You...." Ta fada da qyar,murmushi ya mata kadan yayi kaman yana gyara cuff dinsa saboda yawan cameras din dake saitinsa. "I'm sorry,I thought you would recognize the scents eventually.” "All these perfumes?....you're the owner?" Ta fada softly ta yadda shi kadai zai iya ji,saboda tanason wanke zargin mafarki takeyi daga ranta "For years...." Ya dakata kadan "And now....." ".....your name is on the door". Sai taji jikinta ya yi sanyi.Ba saboda kudin kawai ba.Ba saboda empire din ba. Sai saboda ya boye mata girmansa. Ya sanya sunanta a saman abin da yake alfahari da shi. Kuma bai taba amfani da dukiyar wajen nuna iko a kanta ba. Bai taba qoqarin gwada mata shi wani bane.....saidai ikon ya nuna kansa da kansa a tattare dashi. A iya nan kawai.....yasha banban da tarin mazan da sukasota,sukaso ta kasance mallakinsu. Kowa yana zuwa don nuna mata kansa.....a sanda shi boye mata kansa yake. Sanda ya kama ta fara saninsa kuma.....ikonsa ne ke magana bawai shi ba. Hannunsa ya miqa mata calmly.....yana jin kishinta.....amma yanaso ya cika mata wannan burin daya gani rubuce cikin qwayar idanunta. "Come with me giiftii....." "......You should stand beside the owner tonight." Dukka gwiwoyinta suka sakeyin sanyi,bata da wannan qwarin gwiwar.....bata da wannan power din da zata iya tsaiwa kusa dashi a idanun duniya. Tana jin batakai ba....matsayinta baikai ba,komai nata baikai ba,sai tayi qasa da kanta. "Na gode da wannan karramawar.....amma...." "Is okay....ba buqatar jin dalili,zabinki ne....zan cika miki shi" Sai yaci gaba da takawa yana wucewa zuwa stage din a hankali. "Tashin hankali" Omar.....shi kadai kalmar ta iya fita daga bakinsa,amma dukkaninsu hudun daskarewa kawai sukayi kowa ya gaza cewa komai. Sautinsa kadai ya sanya kowa shiga cikin nutsuwa. Wannan muryar wannan husky voice din da kishinta ya cika zuciyar akhnan ta fara tashi cikin mic din daya karade ko ina. Ya tsaya a tsakiyar stage din cikin nutsuwarsa ta al’ada. Power dinsa baya buqatar hayaniya. Silence kadai ya isa ya sa mutane su saurare shi. Wannan sunan THE SILENCE ONE.....ya matuqar dacewa dashi sama da duk yadda za'a kwatanta. Tarihin gwagwarmayarsa da kafa kamfaninsa na farko....a hankali har zuwa yanzu inda qoqarinsa ya tsaya. Ba mutanen dake zaune kawai a gurin ba.....hatta ita saida tarihin yaja hankalinta. An interesting story da yake dauke da wasu darussa kala kala. Nasara daya bayan daya.....jajircewa.....karbar qaramin matsayi ba tare da duba daga irin gidan daya fito ba,kawo yau yanzun nan da yake amsa sunan WANI. "Before tonight ends......" Muryarsa ta sake ratsa tsakanin maganganun mutane ta kuma wanzar da wani irin shuru daya haifu lokaci guda. "......there is one more thing" Sake daukan shuru hall din yayi. Da wani irin nutsuwa ya sauke idanunsa akan akhnan din. "Maison Akhnan was never built for business alone.” tsaiwa cak tayi itama da nata idanun cikin nasa,tana jin wani abu yana zagaya duniyarsa da tata. "Some names carry value…” ya dakata yana ajiye numfashi. “…and some names carry peace.” sai ya sakeyin shuru na second biyu muryarsa tana bada wani echo cikin hall din. Ya sake dauke idanunsa zuwa kan manyan mutanen dake gabansa. "“Hers carried both.” ya furta kalmar yana maida idanunsa gaba daya a kanta. Idanun nata ta lumshe a hankali tana jin wani irin yanayi. Nauyinsa.....qauna.....soyayya da tarin girmamawar da take ganin bata cacanceta ba. Dukkanin hankula sukayi kanta,manyan baqi dama duk wanda yake gurin,cameras din dai da bayaso da sauri kowanne ya maida tasa kanta. Wani babban labari ne.....wani babban al'amari ne da ba wata tasha da zataso ya wuceta. Zazzafar soyayya a bainas nasi,kai tsaye.....daga bakin babban malamin nan na duniya gaba daya....yarima kuma sheikh muhammad haisam aba jifar. Saidai cikin qasa da minti biyar dukka security din dake gurin suka sanya 'yan press saukar da cameras dinsu,dole kowa ya kasheta ya kuma sauke don samun ci gaba da kallo da idanunsu. (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) A gurin....ji yakeyi kaman ita kadai dashi sune suka rage.... Gurin ya masa fili fayau.....ba wanda yake gani sai ita daya tallin tal. wani elegant black document legal director na kamfanin ya miqa masa cikin girmamawa,yasa hannu ya karba yana riqeshi da kyau. A nutse ya fara saukowa daga stage din,straight zuwa gabanta. "Haisammm" Bakinta yake furtawa sanda yake takowa zuwa gabanta. Shi daya ya gane sunanshi ta ambata saboda kalmar ta fita ne ba tare da sauti a cikin ta ba. Ya tsaya a gabanta,sannan ya rusuna saman qafafuwansa yana dora nauyinsa akan qafarsa ta dama. "You once said this scent felt like memory.....uhmmm?" Ya tambayeta yana dage girarsa guda daya sama. Idanunta ta lumshe.....ya ilahee.....komai da take boyewa,komai da take alkintawa cikin zuciyarta ya sani. Ya akayi?,garin yaya yasan komai game da ita?. Tafin hannunsa ya bude mata saitin fuskarta. Ta dora idanunta a hankali tana kallon kwalbar dake ciki. Wata irin kwalba ta alfarma da bata taba ganin irin design din ba,wadda ke rubuce da LUNE NOIRE ✨. Perfume din da tafi so a duniya ba tare da tasan sunansa ba. Luxury exclusive line. "“You loved it long before you knew who created it.....haka ne?" Ya sake tambayarta wani lafiyayyen murmushi yana fita daga saman fuskarsa. Kasa amsa masa tayi,don gaba daya ya gama qone mata ruwan kai. ".....and now" Ya fada yana gyara tsaiwarsa tsugunnonsa a gabanta Yana qarashe maganan nasa da wnai slow pause ".....it belongs to you" . ".....what?" Ta fada tana fidda idanunta waje da wani razanannen mamaki. Murmushi ya sake sauke mata. "The scents" Sai ya dakata. "The formula" Ya sake dakatawa. "The ownership rights". Girgiza kai tayi a hankali kamar bata fahimta ba. "This is impossible". Ya fahimci rikicewa a tare da ita,sai ya sake rage tazarar dake tsakaninsu,wannan ya sanya security dinsa suka sake rufesu kaman yadda suka musu a dazu,muryarsu ce kawai ke fita. Qasa yayi da muryarsa sosai,kamar da ita kadai yakeson yayi magana duka taron mutanen. "No....." ".....Impossible is the effect you have on me.” ya fada da wani salo daya sare dukka sauran karsashinta. A nutse ya bude folder din. Official signatures. Legal seals. Ownership transfer duka suka bayyana b'aro b'aro. Manyan shanyayyun idanun nan nasa ya daga ya dubeta "As of tonight...." Sai ya dakata. "LUNE NOIRE is yours". Wasu irin hawaye taji sun cika mata idanu.....wasu irin hawaye masu dumin gaske.....Ba saboda kudin ba. Sai saboda yadda ya miqa mata wani b'angare na empire dinsa kamar abu mai sauqi. Ms ta masa?.....me ta mallaka masa?,me ta taba masa data cancanci wannan?. Kasa jurewa tayi.....tambayar ta mata tsaye a wuya,ta ware idanunta da hawaye ya fara jiqe eyelashes dinta. "Why would you do this for me?” ta furta da wata tattausar murya dake nuna karaya sosai a cikinta. "Because some things are too personal to sell to the world.” sai ya dakata kadan yana duban qwayar idonta data masa wani irin kyau,blue din ciki yau na dabanne. ".....wannan turaren" ".......ko yaushe yana tunamin dake.....yana tunamin tsada da darajar abinda na mallaka". Hall din ya sake gaurayewa da qananun sowa. Gani suke kaman wani film suke saurara......duk da basa iya ganinsu,amma maganganunsu sun tsuma kowa. Mamaki ya daskarar da 'yan shidanshi,banda suna iya ganinsa zasuce wani haisam dinne daban. Akhnan kuwa.....bata jin komai yanzu. Sai shi.......sai kalamansa......sai yadda ya d'ora sunanta a kan abin da duniya ke dauka matsayin luxury empire. “…Ya bani fiye da dukiya…ya bani matsayi a rayuwarsa" Abinda zuciyarta ke maimaita mata kenan. *_Wannan farinciki......wannan soyayyar da aka sake tabbatar da ita a gaban idanuwan duniya........wannan walwalar......cikin rashin saninsu......ashe K'ADDARA TANA SHIRIN WARGATSASU A WASHEGARIN WANNAN RANAR......BABBAN TASHIN HANKALIN DA ZAI GIGITA DUNIYARTA....SHIN ZAI ZAME MATA LU'U LU'UN DA HASKENSA ZAI HASKA MATA GABANTA?_* *_LU'U LU'UN DA HASKENTA ZAI WALQA MATA ABINDA KE DUQUNQUNE CIKIN RAYUWARTA?_* *_HASKEN WANNAN LU'U LU'UN ZAI ZAME MATA MAGANI?,ZAI MATA RANA?_* *_muje zuwa da yardar me duka zuwa shafukanmu na gaba_* *zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 08187255862 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 08187255862 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 102* ________________________ *_SHUWA INCENSE AND MORE_* 😊 *_kai daga jin sunan basai an gaya maka ba_* *_kai daga jin sunan basai ka tambaya ko tsaya tunanin maganar me ake ba_* *_MAGANA CE TA GIDAN QAMSHI_* *BAFA GAMA GARIN QAMSHIN DA KIKA SABA JI BA HAJJAJU* *KINA QONA TURARE YANA QAURI* *KINA SAKA KHUMRA TANA BIN SHANUN SARKI* *WANNAN DIN TURARE NE DAKE DAWWAMA A DAKI DA JIKI.....DA SALON QAMSHIN DAKE MANTAR DA ZUCIYA DUK WANI B'ACIN RAI* *TASTED AND TRUSTED👌👌👌100% HAJJAJU* *NA DABANNE A CIKIN NA DABAN*🙌🏽🙌🏽 *idan akazo kan SHUWA INCENSE an tashi magana* *idan ma kinsan baki shirya jan magana ba a duniyar qamshi to kisha zamanki hajajju* *_zaku iya magana da ita kai tsaye ta wannan number wayar_* +234 704 229 3387 _________________________ D'aya bayan d'aya suke shigowa daya daga cikin empty suite din da ya sanya aka ware saboda su cikin Atlantis the royal hote din. Omar ne a gaba.....wanda ya zare blazer dinsa ya jefar "No" Omar ya fada da wani abu cikin muryarsa me nauyi. "Absolutely no" Ya sake fada yana sauke idanunsa akan haisam wanda ke takowa cikin suite a gajiye rungume da suite dinsa 'yar saman. Idanunsa ya dauke daga kan omar yana zama saman daya daga cikin sofas din dake zagaye da qawataccen parlor din. Ba omar kawai ba,tunda suka taho duk da a mota daban daban suka taso,kowa cikin tasa motar amma yana lura da irin kallon da suke binsa dashi. Agogonsa ya fara zarewa kafin ya amsawa omar. "What now?". " Wallahi bakai bane" Naseeb ya karba wannan karon da wani expression na mamaki akan fuskarsa. "This is getting serious fa?" Khadeem ya fada yana yarfa hannunsa shima mamaki kwance akan fuskarsa. A nutse ya ajiye agogon,ya koma yana sassauta tie dinsa gami da bin kowa da kallo d'aya bayan d'aya. "I warned you people....." Maleek daya bude wani gwangwanin lemo ya fada yana qoqarin boye dariyarsa,ya zuqi lemon sannan ya qarasa maganan daya fara ".....love humbles men violently" Dariya suka sanya gaba dayansu,suna tafawa a tsakaninsu. Sai a sannan ya jefawa maleek din harara yana dubansa. "Be quite" Ya fada idanunsa suna lumshewa saboda gaiiya. Bada murya me amo yayi maganan ba,amma a halittarsa ce.....muryarsa tana fusgar hankalin duk wanda yayi magana dashi koda cikin hayaniya ne. "Haisam" Amjad ya fada yana dawowa gabansa ya zauna yana dubansa sosai....kamar wani me daukan karatu. "You adjust akhnan's chair today?" "And you adjust her bracelet?" Khadeem ya fada. "Ko blinking bakayi.....hala baka sani ba....duk wani motsinta yana under control naka....." Mutallab ya fada yana fidda idanunsa waje. "......ga wata irin gabatarwa.......ka gabatar da wannan soyayyar a inda ya dace" Naseeb ya fada yana girgixa kai. "Mu masu aure.......two years ago.....sai naga kaman bamu iya komai ba.....bamusan komai bama ashe" Naseeb ya fada yana watsa hannuwansa fuskarsa tana komawa kalar tausayi. Murmushi ya subucewa haisam din....wani kalan sassanyan murmushi. Ya juya kansa kadan yana dubansu. "You people are overreacting" Ya furta softly yana kallon agogon hannunsa. Tun a gurin ya barta da baqi mata bai kuma sake ganinta ba,saidai ya tabbatar tana under security guard,ba wani abu da zai sameta. Har yanzun da suka sashi a gaba da wannan kalar tsiyar tasu ita yake gani. Sanda take karbar baqi mata a matsayinta na matar mamallakin kamfanin.....kuma shugabar sabon kamfanin da ya zama mallakinta a daidai lokacin da kowa baiyi zato ba. Yadda take tafi da komai cikin tsari da nutsuwa,duk da baiyi mamaki cancan ba sai burgeshi da yanayinta ya sakeyi ya kuma sake dilmiyashi a kogin qaunarta.....ko ba komai yasan ta taba zama.shugabar wani kamfanin samar da suturu na alfarma. "Ko ba overreacting ba?" Omar ya fada mamakin haisam yana sake kasheshi. Har yanzu yana jin komai ne kamar mafarki,har yanxu ya kasa gasgata hakan. "......hmmmm,this from the man who Once said....." Maida muryarsa yayi wani iri yana qoqarin kwaikwayon muryar haisam. "Women complicate focus...." Dukkansu sun tuna,magana ce da yake yawan maimaitata. "And now look at you....." Khadeem ya fada "Your focus literally wearing laffaya". Murmushi ne ya subucewa haisam yana sake relaxing cikin sofa din. Maganan lafayar ya sanya ya sake hangota a wancan awannin cikin baqar lafayar data maidata wani yare na daban. Ta Maidata wata mace ta daban da baka isa ka iya cankar qabilarta ba. Ya yarda d'ari bisa d'ari BUZUWA daban take....buzuwar ma irin tasa.....irin tasa d'iyar sultane Muhammad hammud. Shurun da suka sakeyi suna kallonsa bama baisan sunayi ba. "No" Omar ya fada yana girgiza kai....omar din da haisam din yafi shayar dashi mamaki akan kowa. "He's gone wallahi.....he's gone." Ya fada Omar yana yamutsa sumarsa kamar dan wasan qwallon da aka cinyeshi a wasa. Kusan wasan ya koma tsakanin haisam da omar din,yadda omar din ya gigice yasa suka fahimci shi kadai yasan me ya gani tattare da haisam din aka MATA sama da abinda suka sani. Gaba daya setting room din ya rude da dariya "Welcome to marriage sheikh haisam" Maleek da shi ya riga yasha ta hudashi ya fada. Dama irin wannan ranar,....irin wannan lokacin yake jira daga haisam din. "It's not marriage...." Ya amsa calmly yana jin yadda shauqin son ganinta yake ratsashi. "It's her....." Wani irin ihu suka sanya gaba daya,har omar da zuwa yanzu dariyarsa ke bayyana sosai. "Finally...." Khadeem ya fada kaman me calling attention dinsu. Shuru dakin ya sake dauka kuwa. "Now.....explain your self" Murmushi ya sake subuce masa,sai ya miqe ya zauna sosai yana dubansu daya bayan daya. "I'm not explaining anything". "Wallahi zakayi kuwa" Mutallab ya fada yana nunashi da yatsa. "Yes.....ya kamata....don ka fola da yawa billahi.....not just smiling fa.....BRO WAS STARRING" Ya fada yana kaurara muryarsa da buda hannuwansa kaman me shirin kama wani abun. Wani irin dariya maleek yakeyi sosai,har yana sunkuyawa. Shi ya sani.....yana da falaak a gefansa,ya sani muddin akhnan din jinin falaak ce.....dole haisam ya zauce.....dole ya zauce babu ko makawa. "He has entered the dangerous stage fa....." "......the my wife stage" Omar ya qarasa yana sake qoqarin kwaikwayon muryar haisam din again. "Women are unnecessary emotional responsibilities.” omar ya sake fada da yanayin muryar haisam din. Ya gama fahimta,kawai sun hadashi a nan ne saboda suyi masa titsiye. Ba wannan yanzu yafi buqata ba. Hutu....hutawa yakeso yayi.....so yake yaji duminta,so yake ya jita a gefansa. A yau yadda jininsa ya tsinke dinnan sosai,ya sani zaisha wahalan bacci....zaisha wahala kafin ya iya dauke mata ido a yau. A kwana biyar din daya qyaleta shi kadai yasan yadda yake surviving. Miqewa yayi abinsa yana riqe da rigarsa. "I hate all of you" Ya fada a kasalance yana soma takawa. "No....you loved one person" Sai suka sake saka dariya. Khadeem ya nutsu zuwa serious. "But seriously....." Ya tsaya kaman yana nazari. "......I’ve never seen you this relaxed around anyone.”. Shuru dakin ya dauka,don dukkaninsu kaman tambayar tana ciki kawunansu ne. A karon farko,da fidda dukkanin gaskiyarsa.....bawai kare kai ba,ya jingina da bangon da yake daura dashi,idanunsa sun zama soft sosai,ya motsa labbansa da nutsuwar nan tasa. "She makes noise in my head disappear.” sake shuru dakin yayi. Saboda ko su sun san wannan magana tana da nauyi coming from him. “You people are witnessing the downfall of a proud man.” maleek ya fada yana satar kallon haisam yana boye dariyarsa. "Maleeekkkkk" "Sorry babban yaya.....tuba nake" Maleek ya fada da sauri yana surrender. (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) Matse qwalla omar ya hau yi,duk da na wasa ne amma yayi calling attention kowa. "Our emotionally unavailable Sheikh has fallen.......khadeem muna da meeting.....dole mu nemi aure" Dariya ta kaure gaba daya a dakin,haisam ya kaiwa omar cafka saiya zille.....sai kawai ya bude qofar yana fita yana bar musu dakin. *A K H N A N* Rudewa......mamaki......da shiga shock sosai su shehnaz sun yishi. Yadda suke juya zancan tun daga fitowarsu bayan kammala komai da sallamar tarin investors din dakeson magana da ita tace sai tayi shawara da mijinta duk tana jinsu. Itadai abu daya ta sani,da gaske komai ya tashi daga mafarki zuwa gaske. Shin akwai wani sauran abu yanzu daya rage daga haisam wanda bata sanshi ba?. Wanne irin mutum ne shi me abun mamaki?. Me yasa ya zabi ya boye mata komai?. Me ta bashi a duniya.....me ta mallaka masa data cancanci wannan kyautar?....wannan girmamawar?,.....wannan kambamawar?. "DAME ZAN SAKA MASA?" Tambayar data rasa amsarta kenan,saidai a hankali maganganun aisa suka zame mata kamar wani tsani. "Akhnan......baki da masoyi a yanzu sama da sheikh haisam.....ba don ya mallaka miki dukiya ba,saboda soyayyarki a idanunsa daban take da wadda aka saba gani. Baki da wani abu da zaki bashi akhnan a yanxu.....saidai ki soshi.....kici gaba da sonshi......ki riqeshi ki bashi kulawa. Ki kiyaye mutuncinsa....ki faranta masa.....ki sallama masa kanki.....ki miqa masa komai naki. Kin tsinci LU'U LU'U a cikin juji......kina dab da yasar dashi sultane ya cafe miki shi. Kin kalleshi kina mamakin alfanun da wannan abun me datti zaiwa sultane.....ashe shi ya fuskanci lu'u lu'u ne. Sai yanzu daya wanke mikishi tas.....sannan kimarsa ta sake fita" Ta yarda da maganganunsu d'ari bisa d'ari......amma a yanzun abinda ke damunta shine. Ta yaya zata aminta da haisam ta gamsar dashi d'ari bisa d'ari take sonsa. Ta yaya zai fahimci don Allah take sonsa badon dukiya ba?. Ba don abinda ya mallaka mata ba?,ba don shi din a yanzu wani bane?. Wannan ne ya dameta,bata jima a sassan baqi na residence din ba tabarsu dasu Aanani ta wuce suit dinsu din tace kanta ciwo yake mata. Wanka tayi wai ko zataji sassauci cikin ranta. Ranar farinciki ce a garesu da dukkan me qaunarsu amma wani karyewar zuciya takeju da wani irin weakness. Haka kawai taji kuka takeson yi,saita koma a hankali ta zauna bakin sofa bed ta soma rera kukan. Tana tuna komai data masa a baya.....maganganunta.....raininta da izgilinta. Ta yaya zai gamsu da ita cewar da gaske take?,ta yaya zai fahimci komai ya fara kafuwa a zuciyarta tun kafin tasan komai game dashi. A hankali ya bude suit din nasu da sallama a labbansa kamar yadda ya saba. Duk inda zai shiga,koda ba mutum to zaiyi sallama. Kai tsaye yake takawa yana wucewa cikin dakin yana sake jin shauqin isa gareta kamar ana fusgarsa. Sanda ya buda qofar.....idanunsa suka sauka a kanta sai yaji wani abu ya tsaya masa cak "Kuka?" Ya fada a hankali,saidai kuma sautin ya isa kunnuwanta. Share fuskarta ta fara yi da sauri,bataso ya gani,batason wani abu da zai b'ata wannan mode din nasa,batason wani abu da zai ware wannan farincikin da take gani shimfide saman fuskarsa. *zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 08187255862 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 08187255862 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 103* _________________________ https://chat.whatsapp.com/BkfPzSEDhnsIwyCD8LNGkm?s=cl&p=a&mlu=0 *IDAN KINSAN BA ORDER DIN KAYA ZAKI DINGA SAKAWA BA* *IDAN KINSAN BA BUSINESS KIKE DA NIYYAN YI NA KAWO KAYA DAGA CHINA BA KARKI SHIGA* *_DON ALLAH KARKI BATAWA KANKI LOKACI_* *_Assalamu alaikum my loyal people_* *_Barkanmu da wannan lokaci,kuma barkanmu da warhaka_* *_akwai da dama cikin mata wadanda suke sha'awar yin order kaya daga CHINA zuwa NIGERIA,NIJER,CAMERON,CHAD da GHANA_* *_Amma rashin samun amintaccen company....ko hannun wanda zasu dinga siyan kaya ta hannunsu cikin aminci ya hanasu_* *_To a yau addu'ar da yawa daga cikinku ta amsu,don nayo muku tsarabar kamfanin da zakuyi siyayya ta hannunsu su kuma dora muku kayanku har qasarku cikin aminci ba tare da fargaba ko d'ar d'ar ba_* *_kunsan komai nawa TASTED AND TRUSTED ne,to wannan kamfanin idan akwai abinda yafi TASTED AND TRUSTED ma shine_* *_Baki da fargaba kota sisin kwabo,ni SAFIYYA HUGUMA na tabbatar da hakan_* *_Zaki iya kasancewa dasu group nasu,inda a nan zaki hadu da agent dinsu da CEO nasu gaba daya ta wannan link din,zaki samu bayanansu da komai da ya shafi mu'amala dasu_* *INA ME BAKU TABBACIN AMINCI DA INGANCI DA SAUQIN MU'AMALA DASU DA IZININ ALLAH,BAN TALLATA MUKU SU BA SAI DANA GWADA* *Allah ya dafa mana,yasa mana albarka a nemanmu,ya albarkaci halal dinmu ameen summa amee* __________________________ "Nothing" Ta fada da wannan jaririyar muryar tata me taushi. Qofar ya rufe a hankali sannan ya tako cikin nutsuwar nan tasa. Tun kafin ya qaraso,dukkanin kulawarsa da idanunsa suna kanta. A nutse ya qaraso gabanta,ya kuma tsugunna saman qafafunsa yana riqo hannayenta. "Me ya saki kuka?" Ya tambaya a tausashe yana bata dukkan kulawarsa da hankalinsa. Da sauri ta girgiza kai,amma hawayen da suka sake zubowa sai suka qaryatata. Miqewa yayi a tausashe,ya bata hannuwansa dukka ya dagata daga kan sofa din ya maye gurbinta,sannan ita din kuma ya azata saman cinyarsa. Dararewa kadan tayi saboda guntun towel ne kawai daure a jikinta,amma saita lura hankalinsa ma baya gurin. Hannunsa ya miqa ya tattare mata gashinta zuwa gefen kafadarta daya. "Hey" Ya fadi ganin yadda take qoqarin hanashi kallon qwayar idanunta. "Talk to me" Ya sake fada da wani irin laushi a muryarsa dake fita can qasa. Papers din kamfanin dake ajiye saman dressing table din dake gabansu ta kalla,sannan ta dawo da dubanta kansa. "Me na taba yi maka a rayuwa?" Ta tambayeshi kanta tsaye,blue eyes dinnan nata cike fal da hawaye. Girarsa yadan hade kadan yana duban fuskarta,amma hakan bai hanata ci gaba da magana ba,don tanajin kamar taso kanta da yawa. "Wanne irin alkhairi na taba yi maka.......da zan cancanci wannan girman?". Shuru haisam yayi,kallon da yake mata yanzu ya sauya gaba daya. Wani irin zuzzurfan kallo me cike da taushi . " Na taba rainaka fa...." Ta fada da rauni sosai a muryarta hawayenta suna sauka saman kuncinta "......na taba fahimtarka ba daidai ba...." Ta fadi tana sauke idanunta qasa kunyarsa tana cikata. "Amma kuma kai...." Ta sake fada tana motsa labbanta a hankali. ".....ka bani kuma kana sake bani abubuwan da ban isa nayi mafarkinsu bama". Idanunsa ya lumshe a hankali sannan ya budesu kamar maganganunta sun taba wani guri me zurfi a zuciyarsa. Hannunsa dukka ya sanya yana zagayeta ta gefan cikinta,idanunsa sun sake laushi sosai,qamshin jikinta daya cakude da qamshin shower gel dinta har yanzu suna tashi da wani irin sassanyan yanayi dake assasa wani feelings me matuqar qarfi a dukkanin jikinsa. "Look at me" Ya fada da wani irin laushi. Idanunta ta daga masu jiqe da hawaye,hawayen da suka jiqa dogayen eye lashes dinta suka sanyasu sukayi wara wara tare da nuna ainihin tsahonsu. Babban yatsantsa ya sanya yana dauke mata hawayen softly,yana yi yana sake qarewa kyakkyawar fatarta kallo me wani irin sulbi sheqi da daukan hankali. "“You think too little of yourself ko?" Ya fada yana dage mata dukka girarsa. Girar data burgeta ainun yadda take a cike da baqin gashi,gata dab da ita kuma a yau tana kallon yadda Allah ya qera masa ita da kwantaccen gashin da suka kusa hadewa da juna. "Ba sadaka na baki ba...." Ya fada a nutse "......i just honored my wife" Cak numfashinta ya dakata na wucin gadi. Kalmar MY WIFE din tana sauka saman zuciyarta da wani irin nauyi da kuma kima me yawan gaske. "A cikin wadannan....." Ya sake fada da wata nutsuwa cikin kalamansa da maganarsa.....ya fada din kuma yana maida idanunsa kan takardun dake gefan. "None of this is bigger than your value to me" Me zatayi?,bata sani ba itama,sai kawai ta dora hannunta saman bakinta tana fidda idanunta waje. Zuciyarta na wani mahaukacin bugawa tana neman rasa control dinta. "You look shocked" Ya furta yana murmushi gami da lumshe idanunsa. Yadda ta zare dukkan blue eyes dinnan a kusa dashi haka,sai yaga ta masa wani mugun kyau. Wani raunannen murmushi daya taho hade da kuka tayi "...Because nobody has ever treated me like this before.....sai sultane.......sultane kawai". Kansa ya jinjina a hankali,yana jin cewa koda bai ture sultane ba.....ba shakka shine zai zama mutum na biyu da zaici gaba da girmama rayuwarta har haka. Wani irin taushi da tausayi take gani nata a idanunsa,amma har yanzun tana jin kamar bata samu amsarta ba,akwai abinda takeso ta sadaukar.....akwai abinda takeso ta saka masa dashi,ta tattara dukka dauriyarta ta sake cewa. "Me kakeso daga gareni?" Girarsa ya sake dage mata yana dubanta. "Me kike nufi?" Ya mata wannan kwarjinin daya saba mata,saita sauke kanta a hankali. A yau ta quduri aniyar masa wani abu sabo.....wani abu da zai tambayi kansa AKHNAN ce?. Saita miqa tafin hannunta a hankali tana shigar dashi cikin nasa tafin hannun. Idanunsa ya sauke a hankali yana kallo. Yadda ta hade tafukan hannunsu guri guda,yatsunta suka samu cikakken gurbi cikin nasa yatsun kamar tare aka haliccesu. Wani irin feeling ya ratsashi sanda ta matse yatsun nasu gam cikin na juna. "Ka bani girmamawa...." Ta fada muryarta tana rawa. "Ka bani kulawa......" ".....sannan ka bani abubuwan da ban taba tsammani ba" Sai ta danyi murmushi me ciwo kadan. ".....to ni kuma?" ".....me zan saka maka dashi?". Shuru dakin ya sake dauka.....wani irin shuru da bai bar komai ba sai dubai light dake walqiya ta sakanin curtains na dakin da skyline view din dake bude. Haisam ya zuba mata idanu quietly. Wani irin kallo mai nauyi. Kamar yana kallon abu mai daraja da baya son ya subuce masa. "You already give me more than you realize.” ya furta da muryar rad'a. Kai ta girgiza da sauri " Aah....." ".....wayo ne wannan......ban kuma yarda ba" Ta fada da wata shagwaba data kusa narkar dashi ya sulale yabi kujerar. Komawa yayi baya ya jingina da fuskar kujerar yana neman tallafinta. "You really want to know?” ya tambaya da low voice dinsa. Kai ta gyada a hankali da baby face dinnan nata dake jin rigima sosai. Sai ya danyi shuru,kafin muryarsa ta sauya,Lower and softer. "When I come back tired…” idanunsa still a cikin nata idanun "…look at me the way you’re looking at me now.” sai numfashinta yadan tsaya,saboda yadda ta kulle idanunsa cikin nata. "When the world becomes loud…” ya saki wani miskilin murmushi daya qara masa kyan da taji kaman zai kasheta. "…be the place my mind rests.”. Hawaye kawai taji sun cika idanunta. Saboda yadda yake magana,ba kamar mai neman abu daga gareta ba. Kamar mutum ne da ya samu nutsuwa a wajenta ta har abada. Dawowa yayi ya zauna sosai yana hade gap din dake tsakaninsu. "And......" Kalmar ta sakata sake.maida qwayar idanunta cikin nasa. ".....love me honestly....." Ya qare da fadin "......that's all". Wani nauyi me dadi zuciyarta tayi mata. Wata irin soyayya ce ke mamayar kowanne sashe na jikinta. " Haisamm" Ta kirashi da sound da kuma sunan data lura yana qaunar ji daga bakinta. "Yes ma'am" Ya fada yana kasa jurewa sai daya cusa yatsunsa tsakiyar cinyoyinta biyu yana shimfide tafin hannunsa a kansu gami da sarqe idanunsa cikin nata. "“I think… you’re spoiling me.” ta qwato kalmar da qyar saboda yadda ya soma yamutsa fatar cinyarta a hankali da wani irin yanayi me tada tsigar jiki. (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) "Good......“That was the intention.” ya fada yana sake nutsa jikinsa a nata idanunsa na sauka kan towel din daya soma zamewa daga qirjinta. Maida idonsa yayi fuskarta,still staring at her kamar babu wani abu a duniya da yake son kalla fiye da ita a wannan lokacin. "Khadeejah nah" Ya kirata da wani sound dake nuna zallar mallaka. Sake kusanta kanshi yayi da ita,abinda ya saka zuciyarta bugawa sosai fiye da dazu,saboda yadda suke musayar numfashi da qamshin jikinsu shi da ita. "Akwai abinda nakeso ki fada....." Shuru kadan "Look at me when you say it......kice kina sona khadeejah" Sosai kunya ta rufeta,tana jin kamar ba zata iya ba. Sai ya dan langab'ar da kansa kad'an. Wancan soft needy side dinnasa yana fitowa. "Yes you can" Ya fada yana dago habarta zuwa fuskarsa sosai "I want all your attention on me.” ya furta da wani laushi daya sanyata sake kallon idanunsa ba tare data shirya ba. "Good.....then say it" Ya fada da muryar rad'a sautinsa yana dakushewa kaman yadda mutumin da zaiyi rada yake magana. "With your eyes on mine.” ya sake fada da rad'ar dai. Numfashinta ya fara rawa,saboda yadda yake kallonta kamar kalmar zata zama abu mafi muhimmanci da ya tab'a ji. "I......" Saita kasa qarasawa,hannunsa dayan yasa ya shafi gefan fuskarta yana sake maida mata gashinta gadon bayanta. "Take your time" Ya fadi idanunsa suna lumshe kansu da budewa. Ta hadiye wani abu a maqoshinta,kafin daga bisani ta tattara dukka qwarin gwiwarta,ta kuma sanya idanunta cikin nasa. "I love you....." ".....ina sonka haisam" Ta fada tana rarrabe kalaman. Wani abu ya sauka a zuciyarsa a hankali da wani irin sanyi,duk expression din fuskarsa ya sauya. Wani deep softness ya bayyana a idanunsa,kamar mutumin da ya ji wani abu da zuciyarsa ta dad'e tana jira jinsa tsahon shekaru. Ya rufe idanunsa na sakanni kad'an,kafin ya jingina goshinsa da nata. "…Again." Ya fada da muryar rad'a data zarta can qasan maqoshinsa. "I love you" "Again" Ya sake fada da wani strong emotions "I love you" "Again" Ya kuma buqata. "I love you" Ta sake maimaita masa. "Again" Ya kuma cewa yana jin wata irin yunwa tajin kalmar daga bakinta. "I love you" Ta furta zuciyarta na karyewa da wata irin matsananciyar soyayyarsa. "Again" Ya sake fada jikinsa yana daukan wani yanayi daya sanya ya fara rawa kamar me jin sanyi. "I love you" Ta sake maimaitawa itama tana jin kamar tana rasa control dinta. "Again....please khadeejah" Tata juriyar ta soma yin rauni,saita aza tafukan hannayenta saman nasa da yake riqe da fuskarta. "I....love you haisam" "Again" Ya sake fada yana zabura gami da daukarta cak daga saman cinyarsa zuwa saman gado. "I love you" Ta sake fada tana lumshe idanunta. Zuciyarta tana wani irin bugawa......sannnan tana sake cika da fargaba. Tana jinsa.....sanda ya soma haukace mata. Tana jinsa sanda yake bata haquri. "Yau...zan sake karya alqawarin nanay.....yau bazan iya jira ba biftuu.....bazan iya jira ba my healer.....saikin bani maganin nan.....bazan iya cika alqawarin nan ba yau" Riqeshi tayi sosai,labbanta suna rawa.....amma itama yau tana jin ta shirya fattatakar wannan tsoron. "Na mallaka maka...kaina......komai nawa....naka ne. Daga yau....ko zan mutu bazan sake hanaka ba.....kayi duk iya yadda kakeso" Tayi maganan da tarin jarumta tana qoqarin binne wannan tsoron. "Na gode....thank you" Da sauran godiya a yaren oromo da French batasan adadin sau nawa ya furta ba. Wata irin duniya suka cilla ita dashi.....wata irin duniya dake gusar da hankalin dukka me hankali,sannan ta gusar da nutsuwar wanda yake tutiyar shime nutsuwa ne. Duniyar da ba'a gane komai cikin ta sai abokin tafiyarka zuwa wannan duniyar. Ta lafe kawai cikin qirjinsa kunya na fattatakar ta. Mamaki kuma yana kusan kasheta. Ya akayi komai yazo da sauqi ba kaman wancan lokacin ba?. Wanne tsatsuba da sihiri ya mata daya sanya ta fita daga saitinta tayita sauka daga kan layukan da sai yanzu take tuna komai?. Wata irin nutsuwa ce ta mamaye dakin,sai wannan hasken na dubai skyline dake ratsowa da glass din dakin. Fuskarta na boye cikin qirjinsa,hannayensa suna zagaye da ita kamar wanda baya buqatar ko iska ta raba tsakaninsu. A nutse ya sumbaci saman kanta. "You okay?" Ya fada softly,kanta ta gyada kadan ba tare data daga fuskarta ba daga ni'imtaccen qirjin da takejin duk duniya ba inda yakai mata nan nutsuwa. Murmushi ya saki kadan,yana dan mintsinar mata kumatu. Yar qaramar qara ta saki,ya sake sakin murmushi,kunyar nan tana burgeshi matuqa. Yau din rana ce ta musamman,rana ce ta daban data miqa masa dukkan komai,yayi yadda yakeso....har yaso ya wuce gona da iri,shi kansa yasan hakan. "Still shy?" Ya fada cikin nutsuwa yana leqen fuskarta. Sake boyewa tayi sosai tana murmushi me cike da kunya. "Don't look at me" Matseta yayi kadan cikin jikinsa yana sakin siririyar dariya cike da nishadi "Too late" Ya furta da tsokana a sound dinsa. "......I've been looking at you all night" Wani siririn kukan shagwaba ta sakar masa tana sake narke masa,shi kuma ya lalace da tarairayarta da lallashinta bilhaqqi da gaske. *zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 08187255862 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 08187255862 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 104* _________________________ *_SHUWA INCENSE AND MORE_* 😊 *_kai daga jin sunan basai an gaya maka ba_* *_kai daga jin sunan basai ka tambaya ko tsaya tunanin maganar me ake ba_* *_MAGANA CE TA GIDAN QAMSHI_* *BAFA GAMA GARIN QAMSHIN DA KIKA SABA JI BA HAJJAJU* *KINA QONA TURARE YANA QAURI* *KINA SAKA KHUMRA TANA BIN SHANUN SARKI* *WANNAN DIN TURARE NE DAKE DAWWAMA A DAKI DA JIKI.....DA SALON QAMSHIN DAKE MANTAR DA ZUCIYA DUK WANI B'ACIN RAI* *TASTED AND TRUSTED👌👌👌100% HAJJAJU* *NA DABANNE A CIKIN NA DABAN*🙌🏽🙌🏽 *idan akazo kan SHUWA INCENSE an tashi magana* *idan ma kinsan baki shirya jan magana ba a duniyar qamshi to kisha zamanki hajajju* *_zaku iya magana da ita kai tsaye ta wannan number wayar_* +234 704 229 3387 ___________________________ *W A S H E G A R I* Tana zaune daga bakin skyline view din,sanye da wata cotton gown me dogon hannu,budaddiya me zuwa hade da wani irin tattasau mayafi. Gabanta cup ne dake dauke da coffee wanda ke fidda tururi a hankali. Fuskarta tayi wani irin fresh,tayi kyau,tana jin gajiyar taron da wadda haisam din ya hada mata daren jiya tana sauka daga jikinta a hankali. Saidai kuma can qasan zuciyarta.....can cikin ruhinta sam ta rasa walwalar data dauka zata tashi da ita. A cikin jikinsa jiya tayi mafarki,mafarkin daya razanata matuqa. Taron jama'a anata kuka,sultane yana tsaye a tsakiyarsu sanye da fararen kaya yana lallashin kowa. Shi ya riqeta a jikinsa sosai harta samu nutsuwa,ya karanta mata addu'ar da akeyi idan akayi mummunan mafarki ta maimaita,ya hanata ta gaya masa me ta gani saboda haka sunna ta koyar,saidai ya sanyata ta shiga toilet ta sake alwala ta dawo ta canza side din data kwanta dazun kamar yadda annabi ya koyar. Yanzun mafarkinne ke mata yawo cikin kai. Ya lura da yanayinta,shi yasa yau ko suite din nasu bai bude ba. Ya hana kowa ganinta,shiketa hidima da ita har mamaki da nauyinsa yana kamata. "Kaman ba wannan sheikh muhammad haisam din na duk duniya ba". Ko coffee din dake gabanta yanzu shi ya hada mata,ya kawota nan wani guri na musamman me kama da farfajiya daga gaban benan nasu ta zauna tana hangen gine gine qananu daga qasa. Taga saqon falaak kan sun wuce ita da maleek,bata zaton su shehnaz sun wuce don jirgin yamma kamar zasu bi. "Hello princess" Taji ya fada da muryar nan tasa da take mutuwar so. Idanunta ta dauke daga inda take kalla da zummar dubansa,amma kunyar daren jiya ta hanata,saita buge da sauke idanunta akan wayarta,sanda yaja kujerar dake opposite din tata ya zauna. Girarsa ya dage mata dukka biyun dake nuna alamun tambaya. Kai ta girgiza masa a hankali tana sauke qwayar idanunta, "Ina zuwa" Yace yana miqewa a nutse. Cikin nutsuwa ya shiga dakin,ya jawo locker din da yayi ajiyar tun a jiya,yana jiran lokacin daya dace ya sake mallaka mata ita a matsayin kyauta. Saidai kuma yana kai hannunsa wayarsa ta dauki qara. Fasawa dauko qaramin akwatin yayi.....yayi taku biyu baya yana kallon wayar dake saman bedside. "Ahmad?" Ya furta sunan kamar wanda yake mamakin ganin kiran nasa. A nutse ya taka ya koma ya dauki wayar,sannan ya zauna saman sofa bed din,idanunsa akan wayar tana nuna masa lokaci na qarshe da sukayi waya da ahmad din. Ajiya ne,sanda yake kan hanyar dawowa ya dauki akhnan zuwa taron. Sunyi maganan jikin sultane da yake sake tsanani,ya kuma aike da likita na musamman qwararre da zaici gaba da bashi kulawa,yace da ahmad din. "Idan sati daya ya wuce babu sauyi.....inajin zan laluba qasar da zata iya kula dashi a fita dashi can" Wannan shine plan dinsu na qarshe kuma maganarsu ta qarshe da ahmad din. Sallama ita yake fara yi a duk wayar da zai amsa....saidai a yau sallamar tasa ta tsaya cak ba tare daya iya qarasata ba sanda muryar ahmad ta mamaye kunnensa. Muryar dake cike da wani irin nauyi da rauni dake nuna tazararsa da sakin kuka kadanne. "Sultane ya rasu.....sultane ya mutu" Shine saqon da ahmad ke fada masa da wata irin muryar dake cike da kakkarwa da saarewa. "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un" Shine kalmar data fita daga bakinsa yana jin wani abu yana hargitsewa cikin kansa. Baisan waye ya kashe kiran ba.....shi ko ahmad din,yadai kalli wayar yaga ahmad baya kan layi. A hankali wayarta dake gabanta ta dauki ruri,abinda ya maido da hankalinta kenan kan wayar. Idanunta suka sauka akan sunan dake yawo saman screen din. "Mammina?" Ta furta sunan kamar wadda bata taba ganin sunan a rayuwarta ba sai yau, Tasha kiranta.....amma sanda suka isa Ethiopia,tarin miscal dinta na kwana da kwanaki wanda bata tana biba. Amma a yau,hakanan taji tana muradin daga kiran. Ta daga kiran sanda take hango haisam daga can qarshen balcony din yana takowa da dan nisa kadan a tsakaninsu,duk da a nesa yake amma hankalinsa yana kanta. Ta danna kore.....koren da dannashi ya juye mata zuwa jaa. "Yanzu kinji dadin rayuwarki akhnan?......" Kalmar data fara fitowa kenam daga muryar mammina.....kalmar da akhnan din ta jita da wani irin nauyi ba tare da taji komai daga bakinta ba. "Me?" Ta jefawa mammina tambayar haka kawai tana jin zuciyarta na wani irin bugawa kamar zata rikito daga qirjinta. Shuru ne na second daya....shuru na second dayan da akhnan ta jishi kamar yana daidai da shirun shekara dubu. "Babanki ya mutu akhnan.....sultane ya mutu!" Ta fadi da wani irin qarfi a muryar ta,qarfin da zai gaya maka da anihin zuciyarta yake fita. A karon farko da maganan ta dinga gutsirewa tana shiga kanta a hankali......tana samun mazaunai iri daban daban cikin kanta tanason zama tare da son isar da saqon inda ya dace yaje. "Karya ne" Amsar data samu kenan daga zuciyarta,amsar da taji tafi gamsuwa da ita,ta kuma zabi tayi aiki da ita. "Me kika ce?" "Nace gatanki ya fadi.....ba sultane....sultane ya mutu!" Ta sake maimaita mata kai tsaye. "....sultane ya mutu a sanda kike can yawo a dubai,kina shaqatawa da more rayuwarki ba tare da kin damu kizo kiga jikinsa da lafiyarsa ba.....sultane ya mutu sanda kika zabi miji....kika zabi yawon duniya akan ganinsa....qasa qasa" "Aah mammina!" Akhnan ta fada a tsawace tana jin yadda zuciyarta ke bugawa kwanyarta kamar zata haukace. Wata siririyar dariyar raini ce ta fito daga gefan mammina. "Yanzu kika tuna kina da uba?.....ki dawo kiga gawarsa idan har kina da sauran mutunci da qauna tsakaninku" Sai mammina din ta fashe da kukan da yabar sautin cikin kunnuwan akhnan. Zare wayar tayi a kunnenta,dukkanin ilahirin jikinta yana bari. Number ahmad take nema,shi kadai takeson kira don taji ta bakinsa.....ta bakinsa takeson tabbatarwa,sai taji kawai an zare wayar daga hannunta. Haisam ne tsaye a gabanta,wanda batasan yaushe ya iso ba,batasan yaushe ya qaraso ba,amma tana hada idanu dashi abinda ta gani cikin qwayar idanunsa sai taji kamar yana ce mata. "Da gaske sultane ya mutu" "Haisam.....abbana......abbana ko?" Ta fada tanason samun amsarta ta idanunsa. (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) Bayaso taji ko taga komai daga gareshi. Bai taba rasa iyayensa ba.....amma ya sani duk wanda zai gaya maka wannan labarin ba zaka taba manta fuskarsa sunansa da muryarsa ba. Da gaske mammina ta isa ta amsa sunan MAQIYIYAR SAFEENA.....tunda ta zabi kaf fadin agadez ta zama ta farko da zata gayawa akhnan din babban rashi da faduwar babbban bango daga rayuwarta?. "Bappi na....haisam bappi na" Ta sake fada tana jijjiga hannun haisam dake tsaye kamar wanda tunaninsa ya tsaya gaba daya da aiki. "Bappi...." Ta fada da wata murya data tsayewa haisam cak a zuciya da kunnuwansa. Qarfafar kansa yayi ya taka a nutse yana hade tazarar dake tsakaninsu,ya rungumeta sosai cikin jikinsa zuciyarsa na wani irin bugawa,ya riqe kanta sosai a tsakiyar qirjinsa. Wani irin gigitaccen kuka ta saki,iya bugun da zuciyarsa takeyi ya isa ya amsa mata tambayarta,iya shurunsa ya isa ya gaya mata ya sani....an gaya masa bappi ya mutu,saita sanya hannunta da suke rawa gaba daya ta cukuikuye rigarsa. "Haisam......bappina.....bappi na ya mutu" Ta sake maimaitawa da madaukakin sauti. Cak numfashinta ya dauke daga gangar jikinta,dukka wani qarfi ko garkuwa ta jikinta ta soma kakkaryewa.....qafafunta suka lanqwashe suka gaza daukarta saboda tsaiwar numfashi da kuma wani abu me kama da ficewar ruhi daga gangar jikinta. A razane ya mata wani irin kyakkyawan ruqo cikin jikinsa yadda ba zata fadi ba. Karon farko da wani abu ya sanya gabansa faduwa......wani tsoro kadan ya shigeshi,yadda jikinta gaba daya da tafukan hannayenta sukayi wani irin sanyi. Fuskarta ya riqe da sauri cikin hannunsa,girgizata yakeyi sosai muryarsa tana sauyawa completely. "Babe" Ya fada muryarsa tana rawa. Wani rauni yana bayyana sosai cikin muryarsa sosai,kamar wanda yake hangen zai rasata shima adan qanqanin lokaci irin wannan "Akhnan" Ya sake kiranta yana tattaba fuskarta sosai,saidai ba wani alamun motsi sam a tattare da ita. Da wani irin sauri ya sureta gaba daya,ya soma komawa da ita ciki. Ya tsaya hannunsa yana rawa ya kira security service. "Call the doctor......now!" Ya fada da wani irin murya da tayi amsa kuwa a dukka sassan suite din. Yama manta yana da wani training gaba daya akan irin taimakon gaggawar.....ya manta kansa......ya kuma manta wayeshi. Gaba daya suite din ya shiga motsawa,su shehnaz aisa dake kuka,da sauran ma'aikatan dake sauri saurin hada mata abinda zai taimakawa numfashinta. Idanunsa dukka suna kanta,ko sau daya bai daukesu daga kanta ba,yana ganin kamar idan yayi hakan zai waiwayo ne ya tsinci gawarta. Tana jikinsa....har zuwa sanda likitar ta kammala bata dukkan taimakon da zata bata din. "Zata tashi in sha Allah" Haka kawai yakejin kamar bata fadi gaskiya ba,haka kawai yakejin kamar ba tashi zatayi ba. Komai ya kwance masa,ji yakeyi kaman ba gangar jikinsa bace a jikinsa. A tausashe ya gyara mata zama cikin jikinsa. Bakinsa saitin kunnenta ya kirata. "Khadeejah.......my princess" Sai muryarsa ta sake karyewa "Wake up" Ya fada kamar wanda yake roqonta akan ta bude idanunta. Ganin idanunta a rufe sake karya masa duk wani qwarin gwiwa yake,ganin idanunta a rufe yana sawa yaji kaman duk duniya ta kulle masa qofofinta gaba daya. Karon farko cikin lokaci mai tsawo tsoro ya bayyana sarai a idanunsa,wani abu guda daya daba wanda zaice ya taba gani tattare dashi. Shafa kanta yayi,muryarsa na rawa cike da damuwa. "I'm here....." Sai muryarsa ta sake rauni cikin yanayi na roqo da magiya. "Akhnaann". Kamar taji kiran,kamar sunanta daya ambata yakai har cikin qwaqwalwarta da zuciyarta dake shirin tsaiwa da aiki,saita motsa yatsunta sannan idanunta suka fara motsawa suna yunqurin bude kansu. *zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 08187255862 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 08187255862 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 105* ___________________________ https://chat.whatsapp.com/BkfPzSEDhnsIwyCD8LNGkm?s=cl&p=a&mlu=0 *IDAN KINSAN BA ORDER DIN KAYA ZAKI DINGA SAKAWA BA* *IDAN KINSAN BA BUSINESS KIKE DA NIYYAN YI NA KAWO KAYA DAGA CHINA BA KARKI SHIGA* *_DON ALLAH KARKI BATAWA KANKI LOKACI_* *_Assalamu alaikum my loyal people_* *_Barkanmu da wannan lokaci,kuma barkanmu da warhaka_* *_akwai da dama cikin mata wadanda suke sha'awar yin order kaya daga CHINA zuwa NIGERIA,NIJER,CAMERON,CHAD da GHANA_* *_Amma rashin samun amintaccen company....ko hannun wanda zasu dinga siyan kaya ta hannunsu cikin aminci ya hanasu_* *_To a yau addu'ar da yawa daga cikinku ta amsu,don nayo muku tsarabar kamfanin da zakuyi siyayya ta hannunsu su kuma dora muku kayanku har qasarku cikin aminci ba tare da fargaba ko d'ar d'ar ba_* *_kunsan komai nawa TASTED AND TRUSTED ne,to wannan kamfanin idan akwai abinda yafi TASTED AND TRUSTED ma shine_* *_Baki da fargaba kota sisin kwabo,ni SAFIYYA HUGUMA na tabbatar da hakan_* *_Zaki iya kasancewa dasu group nasu,inda a nan zaki hadu da agent dinsu da CEO nasu gaba daya ta wannan link din,zaki samu bayanansu da komai da ya shafi mu'amala dasu_* *INA ME BAKU TABBACIN AMINCI DA INGANCI DA SAUQIN MU'AMALA DASU DA IZININ ALLAH,BAN TALLATA MUKU SU BA SAI DANA GWADA* *Allah ya dafa mana,yasa mana albarka a nemanmu,ya albarkaci halal dinmu ameen summa amee* ___________________________ Sosai ya sake riqeta cikin jikinsa yana sake jera kiran sunanta,idanunsa a kanta. "Alhamdulillah" Ya fada sanda numfashinta ya tsaya,saidai kuma cike da rauni. Ta ware idanunta fes a kansa,wadannan blue eyes din da suka sake wani irin haske dake birkice da tsoro da fargaba. "Alhamdulillah" Ya fada yana taba qirjinta yanason jin yanayin bugun numfashinta. A hankali komai ya dawo mata,tamkar mutumin da ya farka daga wani mummunan mafarki bayan dogon lokaci. "Bappi...." Ta furta a raunane hawaye suna sake wanke mata fuska. "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un.....Allahumma ajirni fi musibati,wa'aklifny khairan minha" Ya soma maimaitawa a hankali,ba tare daya kula da kukanta ba.....ba tare daya tsaidata ba....ba kuma tare daya hanata yin komai ba. Ya hade yatsunta cikin nasa yana bata support a hankali da wani yanayi da yake kama da yanason dora harshenta da zuciyarta a ambaton Allah. A hankali bakinta ya kama innalillahi din,taci gaba da maimaitawa tare dashi ba qaqqautawa. Bai motsata ba,bai hanata kukanta ba bai kuma tasheta zaune ba,ya barta a jikinsa sunaci gaba da maimaitawa istirja'in a tare. A haka ta soma jin wannan dutsen me nauyi da qarfi daya tokare mata numfashin yana narkewa yana buda mata 'yar siririyar hanyar da zata iya zama.....siririyar hanyar da zata iya numfasawa adadin kwanakin da takeji sun rage mata. "Da gaske kenan.....bappi na ya mutu?,sultane ya mutu?" Ta fada kanta kwance saman qirjinsa,hannunta na riqe da rigarsa kamar tana tsoron duniya gaba daya. Shi kansa zuciyarsa tana nauyi da ganin halin da take ciki. Muryarsa ta zama calm,soft,cike da nutsuwa. Sai yadan shafa kanta a hankali. "Akhnan" Ya kirata yana qoqarin danne nauyin yasa zuciyar. "Ki saurareni" Ba zata iya amsa masa ba......amma kunnuwanta shi suke saurare. Fatanta daya yace mata abinda taji kawai ba daidai bane,fatanta kawai tace masa sultane bai mutu ba yana raye. "Mutuwa wajibi ce akan kowa" Sai ya dakata a tausashe. "Kuma babu wani rai da Allah ya halitta wanda bazai d'an d'ani mutuwa ba" Hannunsa ya sanya yana dago fuskarta daga qirjinsa,yana bin hawayen dake sake ambaliya suna wanke mata fuska da kallo. Yatsansa ya sanya yana dauke mata su. "Nasan akwai ciwo" "Musamman mutum ya rasa wanda zuciyarsa take qauna" Sai ya danyi qasa da kansa yana kallonta. "But akhnan" "Qaddarar Allah bata tabayin kuskure" Ta lumshe idanunta da qarfi saboda zafin da ke zuciyarta. "Amma na barshi.....shima kuma ya tafi ba tare da mun yiwa juna bankwana ba" Ta fadi tana jin zuciyarta kamar zata tsage. Hannunta ya riqe cikin nasa a tausashe,yana matsawa a hankali cikin nuna rarrashi. "Kada ki azabtar da zuciyarki da abinda baya hannunki.” " Allah ya fimu sonshi.....kuma wataran muma zamu bishi,zamuje inda yaje" Sake matse hannunta yayi da salon bata qwarin gwiwa. "Ki tuna...." "....Duk addu’ar da zaki yi masa yanzu zata isa gare shi.” kai take gyadawa a hankali,duk da ta kasa magana sai hawaye kawai dake zuba. "......Kuma idan ya kasance uba nagari gare ki…” ya saki siririn murmushin da bashi da alaqa da farinciki. "Then the greatest gift da zaki masa yanzu…” "…shine ki ci gaba da zama d'iyar da zai yi alfahari da ita.” kai ta sake jijjigawa da qarfi,sai wani kukan ya sake qwace mata. Wannan karon....kuka ne dake sauke mata gami da rage mata nauyin zuciya. Jawota jikinsa yayi a tausashe yana bata kyakkyawar runguma. "Kiyi haquri saboda Allah" "Ki karbi qaddara saboda Allah" Shuru ya sake ratsawa tana jin yadda maganganunsa ke samun muhalli me kyau cikin zuciyarta suna kuma saukar mata da nutsuwa kadan kadan. "Duniya gaba dayanta tafiya ce akhnan...." "Wata rana muma zamu koma ga Allah" Ya sanya idanunsa cikin nata a tausashe. "So while we are still here…” ya jijjiga kansa. "…let us hold onto faith.”. Maganganunsa wadansu taskoki ne masu tsada a tare da ita,wasu taskoki ne masu nauyin da idan aunasu za'ayi cikin ma'auni zasu rinjayi komai dake kanta. Wani irin tauhidi....imani......haquri da karbar qaddara ta gaskiya ta saukar mata. Da taimakon kalmomin nan guda biyu....masu nauyi da tsada da ya maidasu suka zama abun saurarenta daga sanda aka fara shirya private jet dinsu na tafiya agadez har aka kammala. "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un" Da kuma "La'ilaha illa anta subhanaka inni kuntu minazzalimeen" Daga baya ya surka mata da. "Hasbunallahu wa ni'imal wakeel". A dukkan awannin.....awanni masu tsananin gaske a cikin rayuwarta.....awanni mafiya jirkicewa rudewa da fuskantar ibtila'in da bata taba ganin makamancinsa ba.....hannunsa yana cikin nata. Idan har ya zameshi ko ya sakeshi to sallah zasuyi shi da ita. Bai bari su shehnaz sun ganta da wuri ba sai bayan wasu awanni. Batasan yadda yasha kansu ba.....amma dukkanunsu sunyi qoqarin zama cikin nutsuwarsu,saidai ba wadda idanunta ya dakata daga zubda hawaye. Ba shakka sultane uba ne.....ubane har uba game uba da mara ubanma. Bai taba nuna banbanci gazawa ko kasawa ba tsananinsa da akhnan da kuma falaak ba. Sai zuwa dare sannan private jet din ya samu daman tashi dasu. Shuru ne ya sake wanzuwa cikin jet din,sai sautin engine mai laushi da kuma dim golden lights dake cikin cabin. Tana zaune kusa da window ne kawai,amma idanunta basa kallon komai. Ko daga nesa kana iya ganin yadda idanunta suka kumbura da kuka,kukan da haisam yace tayi idan tanaso.....amma karta fadi karta bari zuciyarta ko bakinta su furta abinda Allah bai yarda dashi ba. Tun bayan tashinsu daga Dubai,bata iya zama lafiya ba. Zuciyarta wani zugi take mata,fargabar da batasan ta meye ba tana sake mamayeta. Kowanne minti zuciyarta tana tuna Sultane ne.....kalaman Mammina .......da kuma yadda bata yi bankwana da mahaifinta ba. (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) Haisam kuwa yana zaune kusa da ita. Ba aiki ba kuma danna waya kwata kwata,gaba daya attention d'insa yana kanta. Kowannd motsi idanunsa suna kanta,yana jin yadda tausayinta ke narkar da zuciyarsa. A yau duk wani tausayi nata da yakeji a baya.....sai yaji ya ninka kansa ninkin baninkin,tausayin daya sake narkewa da wata mahaukaciyar soyayyarta da baisan qarfinta yakai haka ba sai yanzu. A hankali sai ya lura hannayenta suna rawa kad'an. Ya motsa a hankali ya dauki gorar ruwan dakr gabasa ya tsiyaya a cup ya miqa mata “Drink something.” ya fada idanunsa cikin nata a tausashe. Ta girgiza kai cikin karaya. “Bana so…” Sai ya matsa kusa da ita kad'an. “You haven’t eaten either.” ya fada da kulawa sosai,bai jira amsarta ba ya d'ora “Your body needs strength.” Ta lumshe ido tana qoqarin hana sabon kukan fitowa. Bata jin a wannan yanayin da take ciki,banda iska akwai wani abu da zai samu daman wucewa ta maqoshinta. Sai kawai ya cire belt d'insa ya matsa kusa sosai,kafin ya jawota jikinsa cikin tausasawa. “Come here.” Ba musu ta kwanta a jikinsa. Bango take buqata a yanzu,majinginar damiwarta. Ta lumshe idanu cikin gajiya da ciwon da zuciyarta take mata. Sai ya rufe ta da soft cashmere blanket,hannunsa na shafa bayanta a hankali cikin kwantar da zuciyar dake cike da firgici “Sleep a little.” ya fada kaman me lallashin jaririn goye,yayi kissing nata a hankali “I’m here" Ya sake fada yana matsa kafadarta cikin bata assurance. Tafiyar awa biyar zuwa shida tsakanin dubai zuwa agadez. Duk lokacin da ta farka cikin kuka sai ta sameshi still a gefanta,still yana riqe da hannunta.....sannan still calm Kamar baya son ta ji tana ita kad'ai. Bayason yaga wannan kewar.....wannan kadaicin cikin idanunta. Inda yana da dama.....inda ya isa tabbas da zai kauda mata wannan quncin da taketa fama dashi,wannan quncin da take kokawa dashi. *A G A D E Z* *Mano Dayak International Airport* Gaba daya yanayi da atmosphere ya bambanta tsakanin Dubai da agadez. A idanunta sai taga sararin samaniya tamkar ya dusashe. Iskar hamada na busowa a hankali,kunnuwanta suka jiye mata wani irin shuru da agadez din tayi. Daga can nesa tana iya jin sautin karatun qur’ani daga masallatai mabanbanta mallaki qasar agadez din daga kowanne sashe nata. Motocin masarautar agadez ne sun cika wajen. Hadimai bayi da masu tsaro. Royal convoy sosai duk saboda taronta. Amma duk fuska d'aya,yanayi daya zaka gani saman fuskar kowa da zaka kalla a gurin. A hankali take takowa matattakalar tana saukowa,da wani irin kasala da mutuwar jiki cakude da matsewar da zuciyarta takeyi. Tazo step din qarshe saita tsaya cak zuciyarta na wani irin bugawa. Karo na farko kenan.....karon farko da ta dawo Agadez ba tare da jin wanzuwar mahaifinta cikin qasar ba. Karon farko data shigo agadez taga ta mata baqi.....ta mata duhu. Wata agadez da a yanzu ba sultane a cikinta....sultane din da zuwa yanzu yayi kwana d'aya cikin qabarinsa. Wata agadez daban take gani cikin idanunta ba wadda ta saba gani ba. Hannuta ya riqe yana sake matsawa softly cikin yanayin bata qwarin gwiwa. "La haula wala quwwata illa billahil aliyyul azeem....Allahumma ajirni fi musibati,wa'klifni khairan minha" Ya fada cikin taushi. Hawayen nan dai da suka kasa yanke mata,sune suka ciccika idanunta,ta motsa labbanta a hankali tana maimaitawa tare dashi,saita fara takawa suna nufar motar dake bude tana jiran isowarsu. *zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 08187255862 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 08187255862 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 106* __________________________ *_Amintaccen gurin siyayya_* *_ingantattun kaya akan ingantaccen farashin da ba irinsa a kasuwa_* *_BONONZA DA PROMO akai akai_* *dukka sai a HUGUMA CLOSET* *Duniyar kayan yara,mata,maza,dukka* *shaddodi,atamfofi,laces,abayas,jakankuna,takalma,agogo,sarqoqi,English wears,night wears,under wears,da duk wani nau'in sutura babba da qarami* *_Karki yadda ayi babu ke.....leqa kiga yadda closet din HUGUMA kullum ke cike da kaya akan farashi me kama da KYAUTA_* *_YAN SARI....YAN REPOSTING.....DA SARAKAN ADO MASU SIYA DON KANSU....DUKKA INA MUKU MARABA_*🤝🤝🤝🤝 https://chat.whatsapp.com/FrqgC0YmUWP4FPmUzYuLJX ___________________________ Hatta da titunan agadez sai data dinga ganinsu wayam,shuru kuma empty. Kamar suma suna kewar sultane ne. Abu daya data lura dashi,.....masu sana'o'i kamar gurarensu duka a kulle yake. Ta lumshe idanunta tana jan iska tana faran qirjinta ya bude ya kuma rage nauyi. Qila suma suna kewarsa ne.....qila suna tayasu jajen rasashi da sukayi. Sanda suka isa gidan sai ta hangi Ahmad,falaak.....morsa safiyya da nannie,suna tsaye daga nesa. Zuciyarta ta karye da wani yanayi me nauyi sanda take kallon fuskar morsa safiyya. Komai sai yake dawo mata a sannan,hirarrakinsu da nanay.....labarin data bata game da rayuwarsu su ukun. Da gaske ne......uwarta ce ita ta haqiqa.....ashe da gaske ne itace mace mafi kusanci da ita duk duniya....ashe da gaske bata da sama da ita. Ta manta mijinta ya rasu......ta taso ta tattako don kawai ta tareta,don kawai ta tallafi rauninta.....don kawai ta raba wannan baqincikin da tashin hankalin da ita. Duk yadda momma takejin tana da qwarin gwiwa sai taji ashe ba haka abun yake ba sanda idanunta suka sauka akan Akhnan. Kallo daya suka yiwa juna da ita kowa ya karanci dan uwansa bai taba fuskanta da shiga tashin hankali kwatankwacin wannan ba. Rauni ya mamaye morsa safiyya,sai ta saka gefan mayafinta tana lullube fuskarta da wani sabon hawaye ya balle mata. Ahmad ne ya fara takowa gareta da sauri. Ta kalli cikin idanunsa.....sunyi wani irin jaaa sosai. Kamar wanda ya rasa baccinsa na wata da watanni. “Akhnan…” ya kira sunansa hannunsa yana rawa amma yana qoqarin bawa kansa wannan jarumtar da tun jiya daya tabbatar ya rasa sultane ta soma kwaranyewa. Kamar jira takeyi,ta soma takawa tana isa gareshi da sassarfa,sai ya rungumeta sosai yana qoqarin danne tasa zuciyar. “bappi ya tafi…” ta fada da rikitacciyar muryar kuka. Falaak ma idanunta cike da hawaye ta tako da sauri,sai ta rungume Akhnan daga gefe. "Komai ya faru cikin sauri.....komai ya faru cikin irin taqaitaccen lokaci,mun rasa bappi dinmu" Ta sake rushewa da kuka tana riqeta. Kowa kasa magana yayi,kowa zuciyarsa ta raunana. Kasa magana morsa safiyyan itama tayi,kallonsu kawai takeyi da idanun da suka gaji da kuka. Tana jin komai kamar almara,tana kallon komai kamar a mafarki. Yau ba sultane......yau ta rasa sultane,daga ita sai 'ya'yanta,daga ita sai abinda suka haifa ita da safeena. Da qyar ta tattaro qwarin gwiwarta,ta taka wajensu a nutse tana rungumesu dukka a jikinta. "Allah ya baku haquri,ku yaiwata karanta hasbunallahu wa ni'imal wakeel". Akhnan ta duqushewa tayi a jikinta tana kuka kamar qaramar yarinya. Haisam danunsa ya lumshe yana jin zuciyarsa na masa wani irin zugi. Yana jin kamar bazai jura ba.....kamar bazai jurewa ganinta haka ba. Yana jin wani rauni da bai taba jin irinsa tattare dashi ba,komai girman tashin hankali masifa ko qalubalen da zai fuskanta. "Itace rauni na" Ya gayawa kansa a hankali yana sake bude idanun nasa ya zubesu akan Akhnan din. "Haisam" Morsa safiyya ta kirashi tana dubansa. "Kamata muje ciki" Ta fadi ahmad yana riqe falaak wadda zazzabi ya rufeta ruf a gurin. Kamar qafafunta ba zasu taku ba,amma haka ya riqeta cikin jikinsa ya bata dukkan support har suka isa ciki. Babban guri ne da aka ware saboda masu shigowa su yiwa matan sultane din gaisuwa. Shiyya biyu ne,na morsa safiyya sai bangaren mammina,rumfarta da jama'arta da suke opposite da daya bangaren da morsa safiyya ke zama. Guri daya ne....amma a kallon farko da idanunka zaka gane akwai banbance babance me yawa a shiyyoyin biyu da suke opposite da juna. Tana zaune.....kamar ko yaushe....kamar kullum......kamar yau din ba wata rana bace data banbanta da sauran ranakun da sukeyi cikin rayuwarsu ba.....kamar bata amsa sunan MAI TAKABA BA.....kamar ba abinda ya hadata da wannan sunan. Suturarta me nuna ado da iko......mutane zagaye da ita da shimfidun alfarma,manya filalluka masu taushi da manyan warmers na alfarma da fulasai na ruwan zafi da kuma ruwan tea. Wayarta na riqe a hannunta,amma sanda suke shigowa saita dauke idanunta zuwa kansu. Kamar an gaya mata ne.....eh.....gaya matan akayi,tafisu......tafisun dake zaune daga hannun damanta,sai tabar komai,tabar duk abinda takeyi tana zube idanunta a kansu. Wadannan mutanen..... Wadannan rayukan da a yanzu sune target dinta. A dunqule guri daya,a cure guri guda. Yadda take kallonsu a hade guri guda dinnan.....haka takeso so samu ta gama dasu rana guda,ta shafe babinsu.....ta mantar da al'ummar agadez labarinsu. Bata yarda me sa'a bace ita.....bata aminta tana cikin matan da sukayi sa'ar zuwa duniya ba sai da aka wayi gari da mutuwar sultane. "Wannan wacce irin sa'a ce haka?" Ta tambayi kanta tana qyalqyalewa da dariyar da har tafisu sai data daga kai ta kalleta. "Qyaleni na daara tafisu.....kinga laifina?,Allah yana sona......ya kalli tsakiya zuciyata ya hutashesheni daga qoqarin daukan ransa da nake tayi amma a banza. Sun saka tsaro me tsanani.....sun saka likitoci duka don su sashi yaci gaba da rayuwa,ashe gawa suke jira......wannan itace damata.....wannan itace damar da nake jira.....kowa sai.ya shiga uku.....saina jefa masarautar agadez cikin uquba da masifa.....wanda ya bini ne kawai.....wanda yayi biyayya ne kawai zai tsira" Ta fada tana girgiza qafarta cikin jin isa da qasaitarta tana cika. Banda bata sha'awar hawa kujerar sultane.....tafi qaunar juya me mulki daga nesa,tabbas tun a asubahin ranar zata kira kanta SARKIN AGADEZ. Ta dauke idanunta daga kan falaak kenan don duban fuskar akhnan,sai idanunta sukayi kuskuren fadawa kan fuskar haisam. Idanunta ta lumshe sannan ta budesu. Idan tace gabanta bai fadi ba tayi qarya.....idan tace zuciyarta bata tsinke ba ta shimfida qarya. Kyakkyawan dan sauri......mallakar qabilar oromo....wannan kyan nasa irin na ubansa ibraheem......ibraheem din da taso mutuwar so amma ya kwashi qasa ya watsa mata a ido......ibraheem din da shine namiji guda daya da taso ta d'and'ana amma ya nuna yafi qarfinta fintinkau.....ibraheem din da har yau har gobe tana muradinsa......amma ta yarda da yace yafi qarfinta har gaban abada...... Ashe wannan dalilin ne yasa take jin wani abu na daban bayan kwarjini duk sanda ta kalli fuskar haisam?. Inama ace ta san haka tunda wuri.....inama ace tasan jinin ibraheem ne.....lallai da ko ranta zata bayar saita bayar wajen hada jiki da haisam din,koda na dare daya ne ta kuma aikewa Ibraheem saqo har masarautarsa. Bata samu cikakkiyar fansa daga ibraheem ba.....banda KHALEED data kashe masa. First born dinsa daya fara haifa kafin haisam din. Ko a yanzun da idanunta suka sauka kan haisam,saida taji wannan yanayin. Kyansa shi da ubansa me kashe zuciya ne sosai.....amma kuma a yanzun......haisam din babban abokin gaba ne.... "Na gode daka kawomin kanka da kanka cikin sauqi......ka gajartamin wahala,basai na gama da yaqin nan ba naje nayi na Ethiopia ba" Ta fada idanunta cikin nasa. Kamar ya karanci komai.....kamar ya karanci abinda take fada,sai ya murmusa kadan yana zare idanunsa daga nata. "Murmushi?" Ta tambayi kanta tana sauke idanunta qasa. "The silent one.......alsaamit" Ta tunawa kanta da title dinsa. Duk sanda yayi murmushi akwai akwai matsala.....duk sanda yayi murmushi tabbas akwai wani abu me qarfi. (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) "Zan fara rusa duka qwarin gwiwarka daga ranar farko daka shigo agadez" Ta fadawa kanta sannan ta ajiye wayarta tana miqewa. Sai shuru ya ratsa gurin,ganin yadda ta miqe afujajan. “Ya tsaya!.” ta fada cikin bada umarni tana nuna haisam dake takowa da cikakkiyar nutsuwarsa. Idanu kowa ya zubawa mammina din,kafin a hankali wasu idanuwan suka koma kan haisam cikin mamaki. Mamakin da kusan zuciyoyinsu ke maimaita maganan mammina tare da kokwanton da haisam din take kuwa?. Akhnan ta maida idanunta data dauke daga kan haisam zuwa fuskar mammina din tanason tantance akan wa take magana?. “Shi ba jinin Sultane bane.” ta sake furtawa kai tsaye tana ware idanuta a kansa da sauran manyan mutane dake gurin da suka zuba mata ido. “Bashi da abin yi a cikin rumfar zaman makokin gidan nan.” ta fadi wannan karon tana haqiqancewa cikin d'aga sauti da son tozartarwa. Kallon kallo mutane suka fara yiwa junansu,mamaki yana kashe kowa. Ba wanda baisan waye haisam a gurin sultane ba....ba cikin agadez daya rayu dasu na watanni masu tsaho ba,suka amfana da abubuwa da yawa nasa ba.....aah har niger gaba daya. Wasu cikin mamaki. Wasu cikin tashin hankali suke kallon mammina din da wani tarin mamaki,wannan raini ne a bayyane,kuma ga surukin Sultane din?,wanda ya daukeshi a matsayin dan cikinsa halak malak. Akhnan ta tsaya cak,kafin idanunta suka sauya a hankali da wani irin ciwon bacin rai daya cika cikinsu. Me mammina keyi haka?,hankalinta daya?,ko kuma duka da rikitar mutuwar sultane ya taba kwanyarta?. Wannan ya sanya tayi yunqurin dawo da ita hayyacinta. “…Mammina.” ta kirata tana dubanta don tabbatar da zarginta. Da sauri ta dagawa Akhnan din hannu tana dakatar da ita. “Zaman makokin nan na iyali ne.....bana baqi ba" Ta fada tana tsaurara harshenta. Wani irin shuru me gauraye da mamaki ya sake cika gurin. Wasu na kallon haisam din,sunaso suga reaction nasa.....saidai ko daya.....ba abinda ya sauyashi,ba abinda ya sauya wannan calmness din nasa......wannan nutsuwar da haibarsa ko daya ba abinda ya canza a tattare dashi. Nauyi taji qirjinta ya sakeyi.....me yake damun mamminan?. Kwanyarta ta dauko kalamanta.na jiya a kanta ta hada da abinda ya faru yanzu. Attack ne.....attacking haisam din take?. Kai tsaye ta soma takawa don isa gaban mamminan.....don ta tuna mata me take cewa,don kuma ta sake tuna mata da mijin waye dama waye take magana a kanshi. Taku biyu tak tayi taji ya riqo hannunta cikin nasa,saidai hakan bai sanya ta waiwaya ba,bai kuma hanata duban idanun mammina din ba wani bacin rai yana wanke mata fuska. "Shi d'in mijina ne...." Muryarta ta fito da wani irin qarfi da iko,sannan ta waiwaya tana duban idanunshi. "Sannan mutumin daya tsaya dani tun daga sakannin da aka bani labarin mutuwar mahaifina da wani irin salo da ba jin qai ko tausayi a cikinsa....." Takai qarshen maganan wasu hawaye na kubce mata. Ta dauke idanunta tana sake maidawa kan fuskar mammina. "Ya tsaya dani fiye da wasu jinin sultane din....fiye da makusantansa". *zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 08187255862 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 08187255862 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 107* _________________________ *_SHUWA INCENSE AND MORE_* 😊 *_kai daga jin sunan basai an gaya maka ba_* *_kai daga jin sunan basai ka tambaya ko tsaya tunanin maganar me ake ba_* *_MAGANA CE TA GIDAN QAMSHI_* *BAFA GAMA GARIN QAMSHIN DA KIKA SABA JI BA HAJJAJU* *KINA QONA TURARE YANA QAURI* *KINA SAKA KHUMRA TANA BIN SHANUN SARKI* *WANNAN DIN TURARE NE DAKE DAWWAMA A DAKI DA JIKI.....DA SALON QAMSHIN DAKE MANTAR DA ZUCIYA DUK WANI B'ACIN RAI* *TASTED AND TRUSTED👌👌👌100% HAJJAJU* *NA DABANNE A CIKIN NA DABAN*🙌🏽🙌🏽 *idan akazo kan SHUWA INCENSE an tashi magana* *idan ma kinsan baki shirya jan magana ba a duniyar qamshi to kisha zamanki hajajju* *_zaku iya magana da ita kai tsaye ta wannan number wayar_* +234 704 229 3387 ________________________ Zallar mamaki kawai ya sauya idanun mammina,ya kuma daskarar da wasu a gurin. Sabon abune ko ace abinda take idanu basu taba gani ba,a gurin wani mutum gama gari ma ya maida mata magana gatsal haka kai tsaye yana duban qwayar idanunta.....ballanta kuma ace ya faru tsakaninta da akhnan?. "Kin manta kina magana da waye?" "Ba manta ba......ina sane.....a cikin hayyacina nake.....abu guda daya na sani shine....bazan bari a rainamin mijina ba.....domin shine gatana.....shi sultane yace nabi.....shi sultane yace na yiwa biyayya......na girmamashi,kuma zan aikata hakan.....bakin raina" . Idanuwanta gaba daya taji kaman zasu fado,wani irin daskararren mamaki ya mamayeta. Ita mammina?,ita akhnan yau ke iya maidawa magana akan sheikh din?. Ita mammina ita akhnan ke iya sa'insa da ita?,a gaban mutane adadin da batasan yawansu ba?. Da hannunsa dake cikin nata ya jawota baya a tausashe. Bayaso.....bayaso ita da kanta ta tsaya tana qalubalantar matar. "Basai kin kareni ba" Ya fada a tausashe,tausayinta qaunarta da kimarta suna daduwa a idanunsa. Ta yarda.....ta amince fa fuskaceta saboda shi. Duk da batasan wacece ita ba.....batasan tarin zalunci da gurgunta rayuwarsu da tayi ba a a binne cikin qasa. Idanunta dake jiqe da hawaye ta daga ta kalleshi. "Mijina ne kai.....bazan kuma bar kowa ya wulaqantaka ko ya tozartaka ba". "Ina dogarai?.....kuzo ku fitarmin dashi daga nan!" Mammina din ta fada da qarfin muryar data isa har inda suke tsaye suna bawa gurin tsaro da kula da zirga zirgar masu shige da ficen zuwa gaisuwa. Cikin mitunan qalilan suka iso gurin,ta sake maimaitawa. "Na zare masa izinin shigowa gidan nan kwata kwata daga yau.....ku fiddashi daga gidan nan". Baiko motsa ba,haka ya matsa hannun akhnan daya fuskanci tana shirin magana. Duk wanda ya kalleshi sau daya cikinsu sai ya sadda kansa qasa. "Allah ya taimakeka....Allah ya qara maka lafiya" Abinda akwai suke fadi kenan suna sadda kansu qasa. "Bai kamata ba....surukin sultane ne fa?" Nannnie dake zaune ta fada,wadda tashin hankali ya sanya jikinta dukka ya kama rawa. "Rufemin baki.....kibar gurin nan......kema daga yau rumfar nan zamanta ya haramta a gurinki.....don baki da gadon sultane,ko kina tunanin bamusan uba kawai kuka hada shi ba!" Ta fada a tsawace. "Koma ki zauna" Haisam.yace da nanay yana takowa cikin kamewa da haiba. Idanu suka sake komawa kanshi,jikinta na rawa ta koma ta zauna tana duban haisam da ya kawo akhnan gefanta ya zaunar da ita,sai ya miqe tsaye yana zube hannayensa a aljihun black silk jubah dinsa. "Ku koma bakin aikinku" Yace da hadiman,wada kamar walqiya suka soma juyawa suna barin gurin. "Duk taku daya idan kuka qara ba tare da kunyi aikin danace muku ba.....a bakin aikinku,sunanku korarru" Ta fada cike da zallar mamaki tana dunansu. Ta dauka zasu dakata da tafiyar,ta dauka zasu dawo su nemi gafararta,amma sai taga ba wanda ya juyo sunci gaba da takawa. "Allah ya gafartawa sultane" Ya fada yana duban nannie "Ameen" Ta amsa hankalinta yana sake tashi da abinda ke faruwa cikin gidan tun kafin a fidda gawar sultane daga gidan "Allah yasa ya huta.....ki zauna a nan tare dasu.....idan kin gaji ko kina buqatar ganina ki kirani,duk inda nake zanzo,karkiyi kuka.....kada kiyi hayaniya....ki huta sosai....zuciyarki ta samu nutsuwa" Ya fada calmly idanunsa akan akhnan din kamar ba kowa a gurin,kamar ita daya ce me rai a gurin. Kanta ta gyada a hankali tana dubansa,tana kallonsa ya taka a nutse yana ficewa daga gurin. "Ba abinda zai sauyata......yanzu za'a fara wasan" Ya furta qasa qasa suna jerawa da abdii da shigowarsa masarautar kenan. Kai tsaye babbar rumfar da ake karbar gaisuwa abdii ya masa jagora,ya hana duk wani security da guard dinsa shigowa cikin gidan. "Me ya faru da manyan falukan baqi na gidan da ake zaman makoki a wajen rumfuna?" Yayi tambayar yana duban maher. "Giwa ta hana,ta hana kowa rab'ar sashen.....muqullin kowanne sashe da d'akuna yana hannunta. Banda dakin ajiyar sultane,maqullin naji tana nema yau tunda sassafe". Kai haisam kawai ya gyada,ba tare da yace komai ba,saboda suna dab da isa rumfar,kuma yaga tasowar wazeer da wasu manyan mutane na qasar agadez din. ★ Daren gaba daya garin AGADEZ ya sakeyin shuru,sai iska me dauke da sanyin sahara dake kadawa . (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) Cikin sashen ya yanke sauka,sashen dake cikin gidan wanda kafin isowarsa ya zamana a gyare cikin control,komai a kintse yake akan tsarin da sukasan yanason ya kasance,bisa jagorancin maher da abdii,wadanda suna daga cikin wadanda basu bar agadez ba ko bayan ya tafi. Shuru akhnan ta sakeyi,tana kwance lamo,tun bayan dawowarsu daga rumfar zaman makoki. Kuka ya gajiyar da ita,zuciyarta kuma ta yi nauyi fiye da yadda zata iya d'auka. Haisam na can tare da mutane da tarin baqi,gaba daya zaman makokin bayan isowarsa sai ya zamana kamar kowa shi yake jira. Shi yake tsaye akan baqi da sauran masu zuwa gaisuwa,don sam ahmad bashi da wannan qwarin gwiwar ko kadan. Duk da irin jarumatar da haisam din ke roqe hannunsa yana gwada masa,amma ya gaza jurewa,ya gaza tsaiwa kaman yadda ya kamata ya tsaya din. Minti daya zaka ganshi zaune.....minti daya zaka nemeshi ka rasa,ya shiga ciki don yayi kuka,sannan ya share hawayen ya sake dawowa cikin jama'a. Ta sake juyar da kanta wani sashen,kowa fuskarsa a galabaice take da tashin hankali,ba wani me sukuni cikakke,amma bata hangi wannan abun ko qanqani ba a kan fuskar mammina. "Me ya sameta ne haka?,meye a zuciyarta?" Ta maimaita tambayar karo na babu adadi. Baqi kawai take karba cikin nuna izza da mulki,duk wasu siffofi da doka dame takaba ya kamata ta kiyaye a musulunce babu ko daya tattare da ita. Hira da zantukan dake tashi a rumfarta sam ba zaka hada dana rumfar morsa ba,wadda ta cika da shuru da nutsuwa,sai qur'anai da ake rabawa me juzu'i juzu'i ana sauka ana sake juyawa wata. Nannie......hairan.....shehnaz.....aisa take hango fuskokinsu,banda ta morsa safiyya da kamanninta suka sauya saboda kuka. Bata hangi koda digo daya a fuskar mammina kalan alhinin da take gani ba. Ama ture ta falaak wadda tun la'asar mummunan zazzabi ya mata mugun kaye,har sai da maleek ya shigo gidan da kansa ya sanya aka saka mata ruwa,ya dauketa zuwa wani sashen daban da aka basu shi da ita,duk da yana da gida a waje,amma shima ya zabi zama a nan saboda ta zama kusa da morsa,shima ya zamana kusa da abokinsa. "Wannan ba tsari bane.....komai na gidan nan a yanzu na magada ne.....bai kamata a dinga bawa baqi daman wanzar da abubuwa ba. Na kwana uku kawai zasu zauna.....a tashesu a bani.maqullan sassan" Haka ta zaunar da sarkin gida tana gaya masa cikin mutane. "Aah?" Akhnan ta furta a hankali tana jin kanta kamar zai tsage. Ta dauko maganganun mammina randa ta kirata gatsal ta gaya mata ubanta ya mutu. Ta sake dauko maganganunta na dazu,ta dauko wadannan tana hadasu guri daya. Kai ta fara girgizawa sanda zuciyarta ta fara raya mata wani abu. "Aah.....bazai yuwu ba" Ta fada tana miqewa ta zauna sosai,sai a sannan hannunta ya dunguri black tea din da haisam ya hada mata kafin ya sake fita sallar isha'in da har yanzu bai dawo ba,yace kafin ya dawo ta tabbatar ta shanyeshi. Qofar aka murda a hankali cikin nutsuwa,wanda tun kafin ya bayyana ma ta fahimci waye da qamshin nan nasa. Ya sauke ajiyar zuciya yana yabawa qoqarin abdii. Nan din ba hayaniyar waje sam....sai soft gold light. Ba wani motsi da zai iya janye maka hankali. Sai tsantsar safety da zakajishi har jikinka. Ninkin masu tsaro ne suke zagaye da sassan,har abun yadanso daure mata kai,amma koda ta tuna a yanzu wayeshi?sai tayi shuru kawai. Da sallama ya shigo,da sassanyan sautin nan nasa da a yau yakejin ya gaji da yin magana gaba daya,yana jin kamar duka kalaman bakinsa sun qare. Tun asali mutum ne shi da bayason koda musu ballantana wani abu daban,amma yau shi da wazeer da manyan dattawa masu yanke hukunci a masarautar sun qarar da awanni suna duba yiwuwar dora ahmad a gobe a kujerar sultane. "Shine daidai....abinda ya dace kenan,a rantsar dashi a gobe,tabbas zai iya,yayi riqon qwarya mun gani,wani jinkirin kuma nashi da fa'ida". Da wannan maganar aka rufe kowa ya sanya hannu,saidai acan idanun wasu yana hangen wani abu da zuciyarsa bata gamsu ba,cikin jikinsa yakejin "Akwai wani abu....tabbas akwai 'yan wata jam'iyyar daban a cikinsu" Saidai a matsayinsa na qwararren me binciken bin qwaqwaf,koda yatsa bai nunawa kowa komai ba. Abu daya ya sani.....duk wani jini na sultane a yanzu yana jin yana wuyansa.....duk wani ahali na sultane a yanzun yana jin alhakinsa yana wuyansa. Lafiyarsu,tsaronsu da kariyarsu....shi kuma zaiyi bakin rai bakin fama,sai inda qarfinsa ya qare. Amsa masa sallamar tayi blue eyes dinta a kansa. Wani zaki take hanga yana takawa da qafafunsa bawai yarima haisam tsura ba. Jarumta takejin labari.....amma a tsaiwar da dukka maganarsa JARUMTAR take gani da kanta tana wakiltarshi. *zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 08187255862 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 08187255862 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 108* ________________________ https://chat.whatsapp.com/BkfPzSEDhnsIwyCD8LNGkm?s=cl&p=a&mlu=0 *IDAN KINSAN BA ORDER DIN KAYA ZAKI DINGA SAKAWA BA* *IDAN KINSAN BA BUSINESS KIKE DA NIYYAN YI NA KAWO KAYA DAGA CHINA BA KARKI SHIGA* *_DON ALLAH KARKI BATAWA KANKI LOKACI_* *_Assalamu alaikum my loyal people_* *_Barkanmu da wannan lokaci,kuma barkanmu da warhaka_* *_akwai da dama cikin mata wadanda suke sha'awar yin order kaya daga CHINA zuwa NIGERIA,NIJER,CAMERON,CHAD da GHANA_* *_Amma rashin samun amintaccen company....ko hannun wanda zasu dinga siyan kaya ta hannunsu cikin aminci ya hanasu_* *_To a yau addu'ar da yawa daga cikinku ta amsu,don nayo muku tsarabar kamfanin da zakuyi siyayya ta hannunsu su kuma dora muku kayanku har qasarku cikin aminci ba tare da fargaba ko d'ar d'ar ba_* *_kunsan komai nawa TASTED AND TRUSTED ne,to wannan kamfanin idan akwai abinda yafi TASTED AND TRUSTED ma shine_* *_Baki da fargaba kota sisin kwabo,ni SAFIYYA HUGUMA na tabbatar da hakan_* *_Zaki iya kasancewa dasu group nasu,inda a nan zaki hadu da agent dinsu da CEO nasu gaba daya ta wannan link din,zaki samu bayanansu da komai da ya shafi mu'amala dasu_* *INA ME BAKU TABBACIN AMINCI DA INGANCI DA SAUQIN MU'AMALA DASU DA IZININ ALLAH,BAN TALLATA MUKU SU BA SAI DANA GWADA* *Allah ya dafa mana,yasa mana albarka a nemanmu,ya albarkaci halal dinmu ameen summa amee* __________________________ Takowa yaci gaba dayi,saidai idanunsa suna kan tray din daya hada mata komai. Ya tsaya cak daga gaban tray din yana kallonsa yana kuma cire agogonsa quietly. Kunyarsa da nauyinsa taji ya kamata,sai ta danyi qasa da kanta,amma ga mamakinta komai baice mata ba. Ya gama cire agogon,ya zare thobe din jikinsa,ya rage raga shi sai fara qal din singlet wadda ke fidda lallausan qamshin nan nasa,sai wani wando baqi three quarter daya haska fatarsa sosai. Sunkuyawa yayi ya dauki tray din gaba days ya fice dashi,minti goma kacal ya dawo da wasu kayan shirye a sama. Kunyarsa da nauyinsa ya sanya ta sake sadda kanta qasa. "Waane mutum?,waane aikinsa?" Kamar ita?,ita kesa young billionaire prince din aiki?,aikinma irin na kitchen?,hidima da ita?. A dazu ya dafa mata baqin shayi......a yanzun kuma bai gaji ba,ya sake dafa shayin ya hado da wata irin nau'in madara. Gefanta ya ajiye shima ya zauna a nutse,sai a sannan ya kulle idanunta cikin nasa. “Come.” ya fada da muryarsa me laushi can qasa. Bata musa ba,ta miqe a nutse tana takowa inda yake,tana jin kamar iska zata kadar da ita. Kanta sarawa kawai yakeyi,ba abinda kuma ya shiga cikinta tsahon wunin. Ta dauka zai ajeta a gefansa ne,sai ya azata saman cinyarsa,ya mata kyakkyawan masauki,ya kuma yi mata kyakkyawan riqo yadda zataji dadin zama. "Bude bakin" Ya fada yana saka spoon cikin madarar. Ba yadda ta iya ta bude dan qaramin bakinta dake dauke da siraran labba,ya fara saka mata madarar a baki tana karba a hankali. D'aci kawai take mata a baki,basuyi nisa ba ta girgiza masa kai. "Na qoshi" Ta fada a hankali hawaye suna cika mata idanu. Bata dauka idan sultane ya mutu zata iya sake rayuwa koda na second daya ba,yau gashi yana iya shan madara a ranar da zaiyi kwana na biyu cikin kabari,albarkacin miji na gari daya zaba mata. Baice mata komai ba ya maida ya ajiye,ya dauki black tea din. "Bismillah" "Bazan iya ba.....na qoshi" Ta sake fada hawayen suna sauko mata. Shuru yayi,saidai yadan b'ata fuska kadan,abinda taji sam bataji dadinsa ba,sai ta bude masa bakin ya soma zuba mata a hankali. Koda tace ta qoshi,sai yadan sake mata murmushi. "Thanks" Ya fada kamar shi ta ciwa abincin ba cikinta ba. “You need rest.” ya fada yana goge mata gumin daya tsatstsafo ta goshinta saboda yadda dumin madarar da maganin gajiyar me kama da black tea ya soma ratsata. Miqewa yayi tsam yana tasar da ita tsaye,ya kama zip na rigar baccinta zai zuge,saita dora hannunta saman nasa tadan riqe. Wani murmushi kadan ya saki,idanunsa cikin nata yana girgiza kai. "Zan rage miki ita ne saboda kiji dadin bacci sosai.....bazan miki komai ba....in fact bazan iya komai ba.... Just hutawa kawai nakeso kiyi" Sake masa hannun tayi a hankali,tana jinsa ya zuge rigar tsaf,sannan ya dauko mata wata cotton vest da wani skirt mara nauyi iyakar gwiwa ta saka. Har saman gadon ya rakata ta kwanta,yaja mata duvet sosai sannan ya tsugunna ya mata lite kiss. “Haisam" Ta kira sunansa a hankali sanda yake shirin sauka daga gadon. "My princess" Ya fada yana tura hannunsa ta qasan duvet din ya riqe hannunta sosai cikin nasa. “Everything feels empty.” ta qarasa fada muryarta yana rawa. A tausashe ya matsa hannunta “Look at me.” A hankali ta d'ago idanunta. “You’ve cried enough for tonigh" Yayi maganar yana sanya daya tafin hannun nasa a gefan fuskarta a tausashe. “…I keep hearing her words.” ta fada hawayen dake idanunta suna gangarowa. Ya gane sarai,tana nufin Mammina. Sai idanunsa suka d'an yi duhu,yana sake jin wani abu me kaifi game da matar......yana sake jin qasa da sati biyu idan bai sanya matar ta karbi hukuncinta ba shi ba d'an babansa bane. Ta kawo geji.....kuma a yanzun ba idanun duk wani wanda zai sanya ya daga mata qafa saboda shi. Qafafunsa ya daga yana haurawa saman gadon,sai ya kwanta sosai a gabanta suna sharing pillow. Wannan ya bashi daman musayar numfashi tsakaninsa da ita. Wannan ya bashi daman jin bugun zuciyarta sosai,abinda yake gaya masa cewa zuciyarta har yanzu bata gama nutsuwa ba.....bata gama haqura ba,sai ya sarqafe yatsunsa da nata guri daya. “She wanted to hurt you.” ya fada da calm voice,yana ganin ya kamata ya sake buda mata tunaninta akan matar. “Don’t give her victory by breaking yourself.” Sai ta lumshe ido a h a hankali,sannan ta bude tana dunan qwayar idanunsa. “I miss him.” sai Haisam ya rufe idanunsa briefly yana jin ciwo da rad'ad'in zubar hawayen nan nata da yaqici yaqi cinyewa da gasken gaske. Kissing goshinta ya sakeyi,ya dora hannunsa saman kanta yana shafa dogon gashinta a hankali da sigar lallashi. “I know.” cikin muryar rad'a ya maimaita. “I know, babe......kiyi haquri....komai zaizo ya wuce.....kuma komai yayi farko yana da qarshe". Kalamansa sun zauna mata sosai cikin ranta,saita cusa kanta sosai da fuskarta cikin qirjinsa. Gurin da takejin bata da sauran gida duk duniya irinsa. Gurin da takejin bata da wata mafaka me daraja irinsa.....gurin da takeji shi dayane yake bata nutsuwa sama da komai duk duniya. Shuru ya sake ratsa dakin,sai ya miqa hannunsa ya dauki bedside lamp dinsa. Karatun qur'ani ya kunna,da sautinsa da qira'arsa dake.nade cikin fitilar,ya daidaita sautin yadda bazai damu me bacci ba ya ajiye ya kwanta kusa da ita cikin nutsuwa,hannunta cikin nasa,kamar yana tsaron duk wani ciwo ko cutarwa da zai iya isa gareta. Nutsuwa da wani tarin kwanciyar hankali suka soma mamayarta,ta sauke wata ajiyar zuciya me hade da sheshsheqa,kaman yadda yaron daya gaji da kuka keyi cikin qirjin mamansa a sanda ta lallasheshi. Bacci yana qoqarin fusgarta,yana qoqarin dauketa daga wannan duniyar zuwa wata taji sautinsa can qasa sosai kusa da goshinta. “No one will hurt you while I’m here.” Sai daya tabbatar ta nutsu ta kuma yi nisa a baccin sannan ya zare jikinsa hankali. A nutse ya wuce bathroom,yayi wanka yayi steaming jikinsa sosai,yana jin duk wata gajiyarsa tana wartsakewa. Yanaso yayi bacci amma bazaiyuwu ya kwanta ba. Bawai don bayason baccin ba.....aah,sai saboda yana jin cewa bacci bai kamashi ba a agadez. Cikin qatar thobe ya shirya black silk. Ya zama dole ya saka black din,saboda yanason ya dinga sajewa da duhun guri idan yaso haka. Hirami ya nada baqi saman kansa,ya masa wani dauri kaman na dankwali. Baiyi shigar don ado ba.....amma idan ka kalleshi sai kaga ya maka wani irin kyau me daukan hankali. Coffee kawai ya iyasha,sai gasashen naman da baifi yanka hudu ba. Yana tsaye yana sipping coffee din yana kallonta,tayi relaxing sosai dukka jikinta ya saki tana fidda numfashi a hankali. Saita masa wani irin kyau,fuskarta tayi fayau,alamun kukan da tasha sosai yana sake bayyana a fuskarta. Tsaiwa yayi gabanta sosai,ya karanta addu'o'i ya shafa mata,sannan ya sake karanta wasu ya tofa gabas da yamma....kudu da arewa,ya sake rage mata hasken dakin,ya sanya takalmansa masu laushi dake boye sautin taku ya juya yana barin dakin. Sai daya tsaya yayi addu'o'i sosai,bayan wadanda suka wuni a bakinsa yana yi duk zaman wunin da sukayi din,sannan ya saka qafarsa a hankali yana fita. Tun daga babban corridor ya tsaya,yana nazarin guards din dake kula da gurin. Qaramin murmushi ya saki,dama ya sani,ya sani kowanne lokaci zaa canza asalin tsaffin guard na gurin. Yasan hakan zata faru,saidai ya riga ya shiryawa faruwar hakan dama. Ta gefansu ya soma wucewa yana karantar fuskokinsu. Ta wani b'angaren kai tsaye zai iya cewa mutanen mammina ne,saidai hakan bai canza komai ba. Da girmamawa suke gaidashi,duk wanda ya aza idanunsa akanshi sai kwarjininsa ya sanyashi sunkuyar da kai yana miqo gaisuwa. "She moved quickly" Ya furta qasan zuciyarsa,zuciyar tasa kuma ta masa sanyi. Yana jin wani qarin qarfin gwiwa da qarin tabbaci.....nasararsa da sauqi zatazo,wataqila ita da kanta zata zame musu tsani zuwa ga nasarar tasa. Ci gaba yayi da nazartar komai,yana kuma taking note akai. A hankali har ya isa treasury wing(baitul mali). (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) Cikin hikima yake karantar gurin. Komai ya canza...komai tsakanin jiya zuwa daren yau. Sabbin lockers.....qarin masu tsaro da dukkaninsu suka kasance sabbin fuska ne,hatta da seal din gurin an canzashi gaba daya. Daya daga cikin masu tsaron ya zubawa wadannan idanun nasa masu cike da kwarjini bayan ya gaidashi,ya lura kaman shi aka dorawa shugabancin dukka guards din dake gurin. A jikinsa yakejin ba dan asalin qabilar Tuareg bane....a yanayinsa yaji dan qasarsa ne Ethiopian,saidai komai nasa kamar ya juye kadan daga asalin qabilarsa. "Ranka ya dade.....giwa ce ta bada umarni" Ya fada kaman ya tambayeshi. Baice komai ba,yadai sake kallon qofar na second daya sannan ya wuce abinsa. Wanda a kallon second dayan ya gama karantar wanne irin qarfe aka sarrafa aka saka tsaron qofar. Cikin qwarewa da sanin sirrantattun hanyoyi na gidan ya wuce kai tsaye zuwa chamber na sultane da yake kaman office a gurinsa. Badon yana tsoro ko akwai wanda zai hanashi isa gurin ba......aah,ko daya. Hasalima kusan tari jama'arsu ne a hanyoyin da suka birkida suka zana jama'ar mammina cikin rashin saninta. Saidai a komai sirri yana da dadi. A komai kuma akwai kad'ar da hankula koda hankulan amintattun daka yarda dasu ne,da wannan salon....da wannan strategy din da yawa ya cimma nasarar ayyukansa. Gurine dake dauke da muhimman takardu.....muhimmam abubuwa masu yawan gaske. Can qasa ya lura da haske,hasken dake gaya masa akwai wani ta ciki. "At this hour?" Ya fada a hankali ba don yana mamaki ba. Yasan daga yanzu zuwa kowanne lokaci komai me faruwa ne. Cikin inuwar duhun ya dinga takawa da wani irin qwarewa,har ya isa bangaren daya lura hasken yafi yawa ta nan. Ba lallai ya iya jin abinda ake fadi ta ciki ba,baya hangowa baisan kuma waye a ciki ba still saboda yanayin tsaro na ginin,don haka ya matsa ya maqala wani abu a jikin glass din,wanda aikinsa shine zuqo magana daga nesa. Ya sake dasa wani abun,sai ya dago hannunsa dake daure da wani abu kaman agogo me dan fadin fuska. Yana dannashi ya kawo haske,ya kuma nuna kalmar connected. Kai tsaye hoton mammina ya bayyana tarwai saman abun. Ba ita kadai ba..... Ita da wasu mutane ne da baisan kosu waye ba har sai daya matso da fuskar agogon sosai sannan. Fuskarsu ya fara bi da kallo daya bayan daya,ya sansu a ido....yasan 'yan cikin masarautar ne....amma kuma bazaice ga irin zurfin matsayin kowa ba. Takardu ne da files baja baja bila adadin saman table din,wasu a rufe,wasu a bude. "Kana gani?" Haisam ya fada qasa qasa yana taba abun kunnensa. Motsin da yaji shi ya tabbatar masa ana gani din,saiya gyara abun muryar kunnensa dayan ya soma saurarensu. "Ahmad zaisa hannu.....ko yanaso ko bayaso kafin rana ta fito a safiyar gobe" Ta fada tana caccaka yatsanta a saman takardun cikin nuna tabbaci da tilashi. "Amma fa.....wannan kaman ba dabara bace me sauqi.....saboda jama'a suna tare dashi,suna yinsa ko don mahaifinsa". "Ina ruwana?......inaso zuwa gobe ku basu dalilin da zasu tsaneshi!" Ta furta muryarta cike da son kanta da kuma gaggawa a al'amarinta. "Kuma ku fara nemo duk wanda yake tsoma baki cikin umarnina......ban damu ba koda kurkukun da muke dashi zai cika mu aro na maqota" Ta sake fada da zafi zafinta. Cutting komai yayi,don iya haka kawai ya isheshi hujjar wannan ranar.....iya wannan ya isheshi tsanin farko. "Kina gaggawa zaituna....kina gaggawa......da alama komai da wuri zai qare" Ya fada can qasan ransa sanda yake komawa sassansa a hankali. Qarar da yaji kadan daga Device din kunnensa ya sanya ya taba kunnen. "Akwai motsin daya dace muyi?,ko akwai abinda ya dace mu dakatar?" Suka tambaya daga can bangaren. "Noo" Ya fada sanda yake murda handle na qofar. "Let her make the mistake publicly.” ya fada sanda ya tura qofar ya sanya qafafunsa. " Abu daya nakeso......adadin mutanen da ta kulle daga jiya zuwa yau dinnan......sannan....duk yadda zaku bada cin hanci ku bayar ta hikima,banason kowa ya wahala,bawa ko d'a.....me muqami ko farar hula". "Done!" Ya fada daga bangarensa,muryarsa na nuna yadda yake enjoying aikin da gaske kaman yadda ogansa kuma ubangidansa haisam din ya karantar dashi ya samu horo kuma daga gareshi. Ya koma ya samu dakin yadda ha barshi,ba wani abu daya sauya. Ya qarasa gabanta kaman me sake bincikar lafiyarta. Bacci take sosai har yanzu,irin baccin da yakeso tayi. Tausayinta ya sake kame zuciyarsa. Baccinta take da nutsuwa da cikakken tunanin shi ne kad'ai safety d'inta,alhali entire palace already entering silent war *_TURQASHI........me karatu?.....akace garin tone tone ko?,kaza take tono wuqar yanka kanta.....muje zuwa mu gani dai. NASARAR ko FADUWA.....wannan shine YAQIN TSAKANIN QARYA DA GASKIYA_* *_WANNAN SHINE BIGIREN DA RAYUWA KE JUYAWA AKHNAN BAYA.....BA AKHNAN KAWAI BA.....DUKA JININ SULTANE MUHAMAMMAD HAMMUD.... WANNAN SHINE LOKACIN DA MAMMINA KE BURI A RAYUWARTA_* *ZAMUJI KUMA ZAMU GANI IN SHA ALLAH* *Hugumanku ce* *zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 08187255862 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 08187255862 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 109* ________________________ *_Amintaccen gurin siyayya_* *_ingantattun kaya akan ingantaccen farashin da ba irinsa a kasuwa_* *_BONONZA DA PROMO akai akai_* *dukka sai a HUGUMA CLOSET* *Duniyar kayan yara,mata,maza,dukka* *shaddodi,atamfofi,laces,abayas,jakankuna,takalma,agogo,sarqoqi,English wears,night wears,under wears,da duk wani nau'in sutura babba da qarami* *_Karki yadda ayi babu ke.....leqa kiga yadda closet din HUGUMA kullum ke cike da kaya akan farashi me kama da KYAUTA_* *_YAN SARI....YAN REPOSTING.....DA SARAKAN ADO MASU SIYA DON KANSU....DUKKA INA MUKU MARABA_*🤝🤝🤝🤝 https://chat.whatsapp.com/FrqgC0YmUWP4FPmUzYuLJX __________________________ *_W A S H E G A R I_* Washegarin da tazo a cikin ranar juma'a. Juma'ar da take babbar rana me dumbin daraja ga dukka musulmi. Safiyar da agadez ta wayeta da wani irin nauyi daga zukatan al'umma da dama da har yanzu sukejin mutuwar kamar yanzu yanzu aka yita. Ba kuma ga iyalan sultane din kawai ba......ga dukka al'ummar agadez din gaba daya. Tun daga daren jiya zuwa safiyar yau din,duka fadar Masarautar agadez cikin shirye shiryen nadin sabon sultane suke. Sannu a hankali har sanda a wannin suka cika,baqi kuma suka fara isowa suna wucewa babban hall da ake nad'i a duk sanda yanayi irin wannan ya faru. Manyan masu ruwa da tsaki ne cikin hall din,manyan malamai da masu fada aji cikin agadez,manyan hakimai da dukka dattawan azbin. Taro ne daya amsa suna taro,saidai duk wanda gurin.....duk wanda zaka gani ba farinciki bane ya kawoshi gurin ba. Motsa hannunta akhnan tayi wanda yake cikin na haisam,hannun da ko sau daya bai taba sakinsa daga cikin nasa.....hannun da gake riqe dashi bayan kowanne minti don qarfafarta a duk sanda take shirin rikicewa......don bata tabbaci a duk sanda takejin bata da wani sauran tabbaci. Yanzun ma matsa hannun nata yayi,a hankali kuma ya furta. "I'm here" Kaman wanda yake tuna mata tana cikin kulawa da kariya. A hankali ya sauke idanunsa a kanta,sannan yabi inda take kalla da idanunsa. Ahmad ne,wanda yake tsaye cikin shiga ta sarakuna,sarakunan abzin irin shigar da sultane yakeyi. Ajiyar zuciya ya sauke a hankali,wani irin tausayinta yana saukar masa. Bashi da nutsuwa ko kadan,sama da yadda bata da ita. Bayason ganin irin abinda yake gani a idanuntan nan. Rashin nutsuwa,tashin hankali,qin cin abinci,bacci ma ya tabbatar banda yana tsaye akai ba zata yishi ba. "Sai yaushe?,sai yaushe zaki haqura?" Ya tambayi kansa yana jin qirjinsa yana nauyi da damuwarta. Idanunta ta sake lumshewa tana jin sanda aka fara karatun wasu daga cikin dokokin masarautawa ahmad don rantsar dashi. "Bappi zai alfahari dashi.......tabbas zai alfahari dashi" Ya furta tana motsa labbanta a hankali. "In sha Allah.....in sha Allah" Ya fada yana sake riqe hannunta a tausashe idanunsa akan ahmad din. Jini baya qarya,koda anso batar dashi,koda kuma anso tozartashi. Yana tsaye ana shirin rantsar dashi......gaba daya ya juye sultane zam. Ya lumshe idanunsa a hankali yana budesu wasu abubuwa suna sake nauyi a zuciyarsa. Muryar wanda keda alhakin jaddadawa sarki dokokin masarauta ya fara tashi,wanda dagashi sai karbar shahadar rantsuwa. "Bisa ga tsarin masarautar azbin......" “…idan babu wani cikas, Yarima Ahmad shine zai hau kujerar mahaifinsa.”. Gaba daya hall din ya dauki shuru,shurun da akan samu bisa al'ada idan dukkan wanda ke da ruwa da tsakin zaben dorawa ko nad'i ya amince da hakan. Idanu morsa safiyya ta lumshe tana kiran sunayen Allah a zuciyarta. Tana sake jaddada girman zatin Allah.......tana kuma sake tsoro zuwa ga hukunci da iya sarrafa al'amura na ubangiji. An dauke ahmad tsahon shekaru tun yana yaro. Wanda tasan ba don komai bane babban dalilin sai gudun zuwan wannan rana ga abokan adawa. Yau ga ranar da ake gudun tazo. Yau ga abunda ba'aso zai tabbata......yau ga qaddarar da ake qoqarin gogeta zata wanzu. Cikin abinda ba gaza minti daya ba sautin taku ya fara cika hall din. Wani taku me nauyi daya dauki hankulan duk wanda yake gurin suka kuma waiwaya zuwa babbar qofar shigowa gurin. Mammina ce mutum ta farko data fara shigowa,cikin black royal tufafi dake bayyana ikon da take neman daukakawa. Daga bayanta kuwa bayine da hadimai masu kula da tsaro na sasannin sultane......'yan sanda harda sojoji a cikinsu. Tsakiyar hall din ta iso,idanunta a bude tarwai "A dakatar da wannan nadin!" Ta furta da madaukakiyar murya tamkar ba macen dake cikin takaba ba. Ta maida idanunta kan jami'an tsaro sannan ta aza akan ahmad dake tsaye. "Hajiya zaituna" Muryar wazeer ta fada a rude tana dubanta. "Dakata!......." Ta fada cikin fusata tana daga masa hannu. ".......Ba za’a dora wanda ake tuhuma da kashe Sultane akan kujerarsa ba!.” a hankali haisam ya lumshe idanunsa sannan ya budesu tar kan fuskar mammina. Yanaso ya gane a wanne jinsi zai sanyata?,yanaso ya fahimci mutum ce ita ko wata halittar dabbar ta daban?. Wani irin girgiza ilahirin hall din yayi,dukkan wasu manyan fada dake gurin suka soma kallon kallo cike da zallar mamaki,qananun surutai suka fara tashi kadan kadan. "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un" Nannie take fada a birkice idanunta dukka a waje. Rawa kawai ilahirin jikinta yake,mammina take kalla,kwanyarta a yanzun tana komawa shekaru talatin baya. So take ta dauko maga wacece wannan mamminan?,....wannan mamminan da suka qyamaci aurenta?.....wannan mamminan da magabatansu suka hana sultane aurenta.....wannan mamminan da ita kanta asali bata sonta.....amma kirkinta ya rinjayeta.....ya rinjayesu gaba daya suka manta da duk wani qishin qishin din bincike a kanta. Maida dubanta tayi ga morsa safiyya,idanunta a lumshe suke tamkar batason taga kowa da komai dake faruwa a gurin,saidai can qasan zuciyarta (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) "Astagfirullah" Take fadi a hankali tana maimaitawa. Daya daga cikin dattawan masu zartawa ya dakatar da yamutsewar gurin,ya miqe yana duban mammina din. "A dakata jama'a.......a saurara" "Ku kamashi!" Ta furta gaba gadi kai tsaye. "Me kike fada?,kin rasa hankalinki ne?" Ahmad ya furta yana takawa gabanta. Dukkanin idanunsa a bude suke tarwai,kamanninsa yana son komawa na wannan almaz din data raina a baya. Murmushi ta saki a nutse tana dubansa. "Koda ka qaraso gurina.....ba abinda zaka iyayimin...." Ta fada tana jin zafin yadda daren jiya duka ta sanya a nemo mata shi,su bugar dashi da kayan mayen daya daina sha,ya sanya mata hannu a wadannan takardun sannan a yau ya tashi cikin maye a gaban kowa,saidai sama ko qasa ba ahmad din ba dalilinsa,abinda ya sanya ta qarfafa zarginta akan lallai akwai wanda ya sanar masa da wani abun,wanda babu wanda tafi maida hankalinta a kanshi irin HAISAM ALSAAMIT. "......ko kunsan tsohon mashayi aka dauko a matsayin yaron sarkinku!" Wani irin hautsinewa gurin ya sakeyi "Ku kamashi!" Ta sake fada saboda duk qaruwar minti daya tana jin kamar delay take jawo mata. Tanaso kafin sultane ya cika kwanaki bakwai a kabarinsa ita ta gama nata aikin. Tanaso kwanakin bakwai din suzo daidai da sanda zata gama hargitsa masarautar kuma ta tashi.daga wannan duniyar data dade qulle a cikinta. Ba wata duniya data taba dadewa haka zaune a cikinta tana jiran wani abu irin wannan duniyar. "Ba zamu bari ku kamashi haka kai tsaye ba" Daya daga cikin dattawan ya fada. ".....akwai hujjojin da suka bayyana qarara suka kuma nuna yarima ahmad yana da hannu a mutuwar marigayi sultane" Wani d'an tittirnan mutum dauke da kaya irin na lawyers da tarin files a hannunsa ya matso gaba yana fadi gami da soma bude wani babban file cikin files din hannunsa. "Wacce hujja kuma?" Morsa safiyya ta furta cikin ba zata tana bude idanunta tarwai a kansu. Idanu mammina ta aza mata......tanaso ko sau daya,ko sau daya wannan fuskar......wannan halittar RAZANI TSORO da FIRGICI ya nuna saman fuskarta. Saidai har a yanzun da take shirin fara yiwa iyalinta d'auki d'ai d'ai ba wannan alamun a tattare da ita. "Rahotannin masu tsaro guda biyu..." Ya sake fada mutumin yana daidaita takardun hannunsa. "An samu tabbacin cewa,a daren da sultane ya rasu,kaine mutum na qarshe daga shiga gurinsa,ka kuma fito da mintuna masu qarancin tazara Allah yayi masa rasuwa" Kallon kallo aka fara yi,kafin mutumin ya dora. "Kuma masu tsaron sashen sultane guda biyu,mafi kusa da dakunansu sun shaida cewa.....sunji sabani tsakaninku kwanaki kafin mutuwarsa" "Wannan qarya ce!" Ahmad ya fada cikin fusata yana motsawa kaman zai kaiwa me karanto bayanan duka. "Ka nutsu.....nan fa ba mashaya bace" Mammina ta fada tana sakin murmushi. "Tabbas haka ne" Muryar hadimin ta ratsa gurin yana matsowa tsakiya. Mahadi.....daya daga cikin mafi kusanci kuma amintattun da aka yarda sukai kusa da dakunan sultane. "Naji sultane yana cewa bazai yarda da wasu abubuwan da yarima Ahmad yakeso ba......shi kuma yana fadin babu wanda ya isa ya masa shamaki da tsarikansa da abinda yakeso" Ya fada da yanayin da ba tsoro ko shakka a tattare dashi. "Hasbunallahu wa ni'imal wakeel" Akhnan ta fada a hankali tana lumshe idanunta,tana jin kamar bugun zuciyarta zai dakata daga aiki. Hannunsa ya sake matsewa cikin nata zuciyarsa na bugawa sosai. Yana kallon yadda matar ta shirya qarya ha'inci yaudara da cin amana,takeso ta gamsar da kowa cikin salo me burgewa. Koda dukka jikinsa kunne ne......ba yadda za'ayi ya amince ahmad zai iya kashe sultane.....to ta yaya ma?,yaron da sultane din kawai ya sani?,shine duniyarsa?,shine kadai ya rage masa?. "An kuma samu wannan" Mutumin yaci gaba da rattabo bayanai yana matsowa kusa. "Menene?" Daya daga cikin dattawan ya fada. "Guba ce......gubar da aka sameta a sassan yarima ahmad,bayan an samu ragowar irinta a matse matsin gadon sultane" Shock kowa ya shiga,wasu suka waiwaya suna kallon ahmad din,ciki harda akhnan da falaak. Ba don sun yarda ba.....sai don yadda hujjojin sukayi hatsari da yawa....yadda hujjojin zasu iya shigar da shakka da kokwanto a zuciyar al'ummar agadez. "Ahmad?....ahmad fa" Akhnan ta fada ita da kanta wannan karon tana matse hannun haisam a nata. "Masarautar azbin tana da dokoki!!!" Mammina ta fada tana dukan table din dake kusa da ita. Shuru ya sake wanzuwa......ta juya tana karbar wata tsohuwar takarda daga hannun daya daga cikin masanan doka na masarautar. *zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 08187255862 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 08187255862 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 110* ".....Doka ta goma sha bakwai....." “…ta bayyana cewa......duk magajin da ake zargi da hannu cikin mutuwar Sultane......” “…za’a dakatar da nadinsa har sai an gama bincike.” Wani irin shuru hall din ya dauka......shurun da kowa ke da tabbaci akan dokar. Kowa ya sani,haka dokar take a rubuce,kuma har yau har kwanan gobe ba abinda ya sauyata akanta masarautar take aiki. "Kuma idan zargin ya shafi cin amanar jini…” ta fada tana dora idanunta akan ahmad dake tsaye dukka jinin jikinsa a daskare. "…masarauta na da ikon tsare wanda ake zargi ba tare da jiran nadin sarauta ba.” "Qwarai kuwa....haka yake a rubuce cikin doka" Daya daga zaune cikin dattawan fada ya fada saboda tsegungumi da suka fara tashi gurin. Doka haka yake a rubuce......amma kuma zukatan wasu basu kwanta da ita ba. "Wannan ba tsari bane......bai kamata ba.....abune da hankali bazai dauka ba" Wazeer ya fada yana dubanta,jikinsa yana rawa saboda tashin hankali ga shekaru,idanunsa akan mammina. Waiwayowa tayi ta kalleshi,ta dade tana jin haushin mutumin,ta dade tana zarginsa akan hana ma ruwanta gudu sosai,tsakaninta da sultane ko kuma cikin fadar,yanzu ya jefa kansa cikin issue din da asali babu shi a tsarin "Duk wanda zai hana a kama Ahmad......tabbas zai shiga sahun wadanda za'a iya tuhuma da hadin bakinsa......ku kama WAZEER......sannan ku kama Ahmad ku tsaresu dukkaninsu". Ta fada tana jin wata power. Fara tattaki sukayi da wani irin energy,kamar wadanda zasu kama wani zaki. "Aah.....bazai yuwu ba!" Falaak data kasa jurewa ta miqe tana fada dukka jikinta yana rawa. Tsam morsa safiyya ta miqe.....ta damqe hannunta falaak cikin nata tana zaunar da ita. "Ki nutsu falaak.....ki nutsu....me laifi shike tsoron kamu.....kamun Allah kawai muke shakka,don duk wani kamu na duniya ya biyo bayan na sarkin sarakuna!!!" Morsa safiyya tayi maganan da dakakkiyar muryarta da ba tsoro ko shakka a ciki. "Ahmad jinin safeena ne.....jinin safeena ba tsoro a cikinsa.....jinin safeena halastaccen jini ne da ba abinda ya isa ya batashi ko ya gurbatashi......tana tsarkakakkiyar haihuwar da ba wanda ya isa ya taba wannan nasabar!!" Ta sake fada da muryarta data amsa a kowanne sashe na hall din. Saqonta yakai.....saqonta ya isa zuwa duk inda takeso ya isa. Ahmad da mammina,mamminan da ambatar suna safeena yaje ya mata tsaiwar mashi a zuciya. "Dole na haramta kiran wannan sunan a gidan nan.....dole na shafeta har a bakinsu" Ahmad kuma maganganun sun sake daukan hankalinsa zuwa ga morsa dinne. "Haisam......" Akhnan da bata fahimtar komai ta fada tana matse hannunsa da qarfi. Ahmad kawai take gani.....kuma ahmad ne kawai bataso a tafi dashi yanzu......wannan kawai shine matsalarta ba komai da ake tattaunawa ba. "Pleeeaseee" Ta furta tana juyowa gareshi,fitar kalmar ya hade da fitar hawayen idanunta. Shi kadai ne take da hope.....shi kadai ne take da fatan yana magana komai zai canza. Idanunsa ya daga a hankali ya zubewa ahmad su. Wani irin kallon kallo a tsakaninsu na tsahon wasu sakanni. "The investigation should continue......and the low should proceed". Ji tayi kaman ya sanya hannu ya zabga mata mari. " What?" Ta fada a gigice kunnuwanta suna kasa yarda da abinda taji. Kai ya gyada mata a hankali ba tare daya kalli cikin idanunta ba,don bazai iya kallon idanun nata ba. "Idan har shi bame laifi bane.....gaskiya zata wankeshi" Ya fada Kai tsaye da wannan tarin nutsuwar tasa. Yayi maganan ne idanunsa akan mammina.....yayin data sakar masa wani murmushi. Murmushin da zuciyarta ke yaudararta tana gaya mata ta fara nasara.....kuma itace da nasara har abada. Taku suka sakeyi guard din don isa gareshi dauke da handcuff. "Ku dakata!" Morsa safiyya ta furta cikin wani irin zafi. "Karku kuskura.....karku soma sanya wadannan qarafunan a hannun sarkinmu na gobe!" Kaman an watsa musu ruwan sanyi haka karsashin kowa a cikinsu ya ragu,sai suka dakata suka tsaya cak da abinda suke shirin yi din. "Ku tafi dashi cikin girmamawa......jinin sultane ya wuce qasqanci.....gobenku zatazo muku dashi a matsayin sarkinku.....sarkinku na agadez.....kada ku manta da wannan" Ta qarasa maganan tana zube idanunta cikin idanun mammina. Wani kallon kallo ne ya wanxu tsakaninta da ita,tamkar tana bawa mammina tabbacin INDE INA RAYE BA ZAKI CIMMA NASARA BA. Yayin da mammina ke fadin MAMAKIN QARFIN HALI DA TAURIN KAI IRIN NAKI SAFIYYA!. Kuka falaak ta saki wanda ya gauraye ilahirin hall din,akhnan tayi yunqurin miqewa zuwa ga d'an uwanta itama sanda guard ke zagayeshi. A tausashe haisam ya jawota zuwa jikinsa yana mata wani kyakkyawan riqo. "Hasbunallahu wa ni'imal wakeel" Ya fada rada mata a kunnenta,abinda ya sanya jikinta dukka ya sake da wani irin kuka da laushi da zuciyarta tayi,tayi luf a qirjinsa tana jin sautinnan nasa yana ratsa kunnenta,zuciyarta kuma tana mata zafi na yadda yaqi yin komai akan tafiya da ahmad din. Matsowa gabansa tayi kadan,boyayyen murmushin nan da shi kadai yake iya ganinsa ta saki. "Thank you for respecting the law of this palace". Ta fada ne da yaren oromo,a yau din,kanta tsaye,muraran ba tare da tsoro boyewa ko shakka ba. A yau ta amsa ta yarda ita din 'yar qasad Ethiopia ce.....a yau ta karbi wannan "WATA BABBAR NASARAR" ya furta a hankali yana aika umarnin datse wannan sautin cikin muryarta da yaren oromo. *B A Y A N A W A H U D U* Abubuwa da yawa suka faru cikin masarauta a wadannan awannin hudun da sukazo masa da tarin matsi da wahala. Bawai wahalar aiki bincike tattara bayanai da hujjoji ba....aah....sam. Hasalima komai wahalan aiki yana samun wani karsashi da qwarin gwiwa wajen aiwatar dashi. Abu daya da ya sanya wannan gajiyar da wahalar shine. Tarin tuhuma da zuciyarsa keta aike masa kan HAWAYEN AKHNAN. Me yasa baiyi komai akai ba?,zuciyarsa ke tuhmarsa. Me yasa zaibar hawaye masu nauyi cikin idanunta?. Duk inda ya jefa idanunsa sai yaga masarautar kamar ta hargitse. Ba kuma kamar bane....a hautsine din take,ba wai don yawan jama'a ba.....aah. Hasalima ba wani baqo da aka sake bari ya shigo masarautar tun bayan wadancan awannin. An kammala sadakar ukun sultane......mammina kuma tace a dakatar da zuwa karbar gaisuwa ya isa hakanan. A yanzu lokacine na iyalinsa,lokacin iyalin daba wanda ya fahimci me take nufi da hakan,don bayan tsare yarima ahmad wanda labarin ya matuqar girgiza masarautar saidai ba wanda ya isa ya magantu.....ta tsare WAZEER an kuma kama mutanen da suke da fada a ciki cikin fada sun kusa su goma. Shi ya hana maleek shigowa cikin masarautar gaba daya,duk da yace bazai fita daga agadez yabar matarsa ba. "Na maka alqawari.....bakin rai bakin fama. Zan kula da falaak kamar yadda zan kula da akhnan,ba falaak kawai ba.....dukka jinin sultane da iyalinsa gaba daya sun rataya a wuyana" Yasan waye haisam.....ya kuma gasgatashi ba na jiya ko yau ba. Idan yace zaiyi IN SHA ALLAH kaman yadda ta zame masa jini cikin dukka maganganunsa.....to zaiyi din. Idan yace bazaiyi ba.....zai wahala wani abu ya sauya matsayinsa akan wannan. Ko a yanzun da yake takawa zuwa cikin gidan,dab da magariba ne da yanayin yammacin ya sake sanyayar da masarautar dama jikin dukka wanda ke rayuwa a cikin ta. Saidai akwai mutanen da idanunsa suke nuna masa. Ba wannan kamannin sam a tattare dasu,mutanen da ya sanyawa kowanne d'aya daga cikinsu jan fenti. "Abeer......hold on" Ya fada a nutse yana zurfafa kallonsa tsakanin wasu shuke shuken dogon yaro masu tsaho sosai,inda yaga gilmawar wani motsi. Motsin da tuni yayi marking nasa......kuma ya fahimci akwai wani ta gurin. Cikin jarumta da dakewar zuciyar nan tasa yake matsawa gurin,dab da zai isa ya dakata yana ci gaba da zubawa gurin idanu,yadan dauke kansa yana jan numfashi. "Fito" Ya fada calmly,yana kuma sauke maganansa ta bayyana. Tafisu ce,saidai bada wannan shigar tata ta asali ba,da wani launin kayan na daban,fuskarta a lullube da yanayin da ba lallai ka gane ita bace,amma shikam,ba wani motsi ko gilmawar mutumin daya sani da zata boye masa. "Ta shirya korar nannie daga masarauta a daren yau da mafi munin sharri....." Shuru yayi yana zubawa tafisu idanu,hannunsa zube a aljihunsa. Cikin nutsuwar nan daba abinda ke girgizata ya motsa labbansa "Yayi kyau.....yayi daidai,na gode,zaki iya komawa....amma haduwa ta gaba.....a wani gurin daban,ba cikin masarautar nan ba" Qasa tayi da kanta ba tare data iya dagowa ba,har zuwa sanda ya juya yana shigewa ciki. "Abeer" Ya kirashi softly. "Ranka ya dade" Ya amsa masa a girmame. "Nannie zata bar masarautar nan,daga yanzu zuwa kowanne lokaci,a shirya mata sashenta itama.....a shirya mata gurin zama" "An gama". "And then....." Ya fada da yanayin daya karkato da hankalin abeer din. "Sir...." Ya fada don nuna alamun yana saurarensa. "....don't let anyone suffer" "Done sir" Ya fada da girmamawa. "Ina jabeer?" "Yana online". " Cut the connection abeer.....jabeer ina jinka" Ya fada yana ci gaba da nufar sassansa. Nufar da yakeyinta amma yana jin kamar ba tafiya yake ba. Yana buqatar sirri,dole yayi maganar akan hanya ba cikin daki ko wani gida ba. Ya saba idan yana aiki irin wannan.....koda katangu da bishiyoyi baya amanna dasu,yafi ganewa yawo cikin iska har zuwa mission dinsa zai kammala. "She started already sir......" Jabeer ya fada dukka muryarsa tana nuna bacin ransa. Yasan bacin ran jabeer qwarai,wannan ya sanya aikinsu na farko da yasan yana buqatar haquri.....da daukan dogon lokaci kafin bincike ya kammala sai bai sanyashi ba. "💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 111* Jabeer" Ya kirashi da wata murya me taushi cike da tarin nutsuwa,tamkar ba shine yake fuskantar abu irin wannan ba. "Don't forget jabeer.....karka manta" Ya tuna masa da yarjejeniyarsu,alqawarin danne fushi da janye dabi'arsa ta gaggawa cikin aikin kafin ya aminta ya shigo dashi ciki "In sha Allah sir...." Ya fada a hankali. Shuru ya ratsa tsakani,ya kuma bawa jabeer dinne space ya shaqi iskar nutsuwa. "Zaka iya ci gaba?" Ya tambayeshi a nutse. "Yes sir....." "Ehnnnn.....what did she take?" Haisam ya tambayeshi idanunsa suna kallon shimfidaddun duwatsun gurin kamar meson tantance nau'in wanne dutse aka fasa aka samar dasu,iskar yammacin me cakude da sanyin hamada da Sahara da ruwa ya jiqa tana busowa. "Treasury access.” sai ya dakata kamar fadin kawai ciwo yake masa. "Archive wing too.” idanunsa haisam ya dauke daga kan duwatsun a hankali yana duban gabansa. Ba wani mamaki saman fuskarsa,kaman dama yasan zata aikata hakan. Already ya riga yaga alamun faruwar hakan,tun a jiya. “Should we interfere?” jabeer ya tambaya cikin zaquwa. Kai haisam ya girgiza masa a nutse. "No" Ya amsa masa a hankali. Da sauri jabeer din yace. "But if she gains control over the palace records......". " She thinks power is in keys....." Ya fadi wani kasalallen murmushi yana subuce masa. "Let her" Ya fada da wani irin confidence a muryarsa.. "The more confident she becomes…” ya sauke numfashi. “…the more careless she’ll be.” wata nutsuwa ta saukarwa jabeer,sai ya gyada kansa sosai. Sai yanzu ya fara fahimtar ogan nasa..... isn't defending......he's trapping. Ya murda handle na qofar bayan ya wuce dukka faluka,ya kuma duba duk inda ya kamata ya duba din. Ya sallami birra a falon qarshe bayan ya karbi record na awanninta tare da akhnan din. A kwace take kawai,saidai bata banbamce a wacce duniyar take rayuwa a yanzu?. Ba abinda ke mata yawo a yanzu cikin zuciya da idanunta sai yadda aka wuce da ahmad zuwa prison. Prison fa?......abun yana mata nauyi da yawa. Yayin da zuciyarta ta cika da mamakin data dinga ji kamar zai hallakata akan mammina. "Me yasa ta koma haka?,me ya sauyata?" Ta dinga maimaitawa cikin kanta. Maganganunta.....kallonta.....ayyukanta dama idanunta. "Ko ta qullaceni ne?,ko tana jin haushina ne shi yasa take shirya komai?,shi yasa ta shirya hucewa akan ahmad?,saboda me?,me nayi?,don naqi bin tsarinta ne?,don naqi bin umarninta ne?,don na karbi zabin sultane hannu bibbiyu?,me yasa ta zabi ta zama haka?,me yasa ba zatayi komai a kaina ni daya ba?". Sai ta runtse idanunta da gaske tana sake dawo mata da komai akan mammina. Sai kuma ta soma girgiza kanta. Abinda take gani a idanun mammina ya d'ara wannan......abinda take gani a fuskarta yana gaya mata ba iya wannan bane.....ba iya matsalar kenan ba. Idan iya itace ina ruwan wazeer daba ahalin gidan ba?,ina ruwan sauran mutanen da aka gayawa morsa dazu suma an kamasu?. Ta sake rufe idanunta tana dawo da fuskar mammina. Fuskar babban MAQIYI take gani yanzu shimfide a tare da ita. "Me yake shirin faruwa?" Ta tambayi kanta tunaninta yana hargitsewa,ta kuma yi tambayar daidai sanda haisam ya buda qofar da sallama a nutse. Idanunta ta maida ta kulle a hankali. Zafinsa take so taji.....haushinsa take so taji koda d'an kad'anne amma zuciyar taqi karbar wannan yanayin. "Me yasa ba zakiji haushinsa ba.....me yasa?" Ta tuhumi kanta,idanunta a lumshe amma tana jin takunsa da sake kusantotan da yakeyi a rubuce cikin zuciyarta. Duk da idanunta a lumshe suke....amma tana jin hakan a qasan zuciyarta. "Assalamu alaikum warahmatullah" Ya sake maimaitawa bayan wadda yayi da farko bata amsa ba,ya sake maimaita sallamar a sanda ya iso dab da bakin gadon inda take kwance,ya kuma tsugunna a gaban gadon saitin kanta. Bata motsa ba,bata kuma amsa masa ba,sai ya miqe tsam yana isa ga tarin jerin abincin awannin duka da aka ajjiye mata. Suna nan kamar yadda birra ta gaya masa,daidai da ruwa kadan tasha. Ya waiwaya ya sake kallonta,ko motsi har yanzu batayi ba,ya sani....idanunta biyu,ba wani motsi nata da zai boyu a idanunsa. "You didn’t eat.” ya fada softly bayan ya dawo gefan bedside drawer ya zauna daf da ita. Zuwa sannan zuciyarta ta game matsewa guri daya. Zuciyarta tana gaya mata bai kyautu taqi kulashi ba....bai kamata taqi amsa sallamarsa ba. "Ka damu ne?.....tunda ka bari suka tafi dashi" Ta fada da raunanniyar muryartan nan dake kakkarya masa zuciya da katse masa duk wata jijiya me amfani dake jikinsa. Idanunsa ya lumshe yana jin nauyin kalmar qololuwa har cikin zuciyarsa. Ya kamata yayi magana.....amma yanajin kuma ya dace ya barta ta furzar da komai dake cin zuciyarta don samun sassassauci "Na kalleka.....da tunanin zaka hanasu" Ta fada muryarta tana rawa. Shuru yasake ratsawa kaman ba zai amsa mata ba,kafin ya kira sunanta. "Gate up" Ya fadi yana miqa mata hannunsa. Ta riga ta bude idanunta,ya kuma kulle idanunsa cikin nata,bata da daman iya musa masa,yana da wani power na iya sarrafa tunaninka ta idanunsa. Ta miqa masa hannun,shi kuma ya daga ta a hankali ta zauna sosai,ya saka mata pillow ta jingina tana fuskantarsa. A ransa....yake yabawa da yanayin fushinta,da alama ba zata zama me dogon fushi ba,zata zama me bada daman kare kai da kuma saurare. "Giiftii" Ya kirata da girmamawa cikin muryarsa. "Kinaso na hana a tsare ahmad ne?.....ko kinaso gaskiyarsa ta bayyana?". Tambayar ta sauka kwanyarta da nauyin daya sanya ta shiga qoqarin farfasa maganar da kuma dogon nazari. Ya sauke ajiyar zuciya....haka yakeso,maganansa yakai inda ya dace. "Zan iya fidda ahmad a yanzu......zaiyi free.....amma bazan iya wankeshi a idanun kowa da kowa ba.....wanne kika zaba a ciki?" Shuru tayi,shuru me nauyi,shuru me hade da kunya. "He's a genius" Ta fada can qasan ranta. "Akhnan" Ya kira sunanta,sai ta amsa cikin karyewar zuciya da jin nauyinsa. "Na'am" "Na bari suje dashi......because some wars....are not won the moment they begin.” a nutse ta daga kai tana kallonsa,sai takejin wani abu cikin muryarsa.....cikin maganarsa wani sound da ma'ana yake bayarwa daya dasa wani abu cikin ranta. Yadda yake maganan,sai takeji a jikinta akwai wani abu......akwai wasu abubuwan daya sani fiye da kowa. Hannunsa yakai kan fuskarta yana share mata hawayen da yayi saura softly. "I would never stand with someone against your family.” maganan ya ratsa har can qarqashin zuciyarta. Idanunta na yawo saman fuskarsa,kamar zuciyarta ta fara gaya mata akwai wani abu me zurfi. "I would never stand with someone against your family.” kalaman suka sake dawo mata tartar!. Tasan gaskiya ne,tasan baya qarya....komai ya fada zai tsaya a kanshi,baya sauya magana ta dade da sanin hakan. "But Ahmad is alone there…" ta fada a hankali. Dan murmushi ya saki me laushi,ya sani,ta fadi abinda yake cin ranta ne. "No.....he's not" Zuba masa ido tayi tanason gane ma'anar abinda ya fada,saidai bata buda baki ta tambaya ba,shima baice komai ba sai idanun nan nasa masu nauyi daya aza mata. Daga qarshe ya janyesu daga kanta,saboda wani yanayi da yake fusgarsa a tattare da ita,wanda yasan a wannan yanayin.....a wannan lokacin komai bazai yuwu ba. A wannan yanyin tana buqatar space sosai da hankalinta zai nutsu ya tattaru guri daya,don haka sai ya miqe,ya isa ga tray din. Tsayawa yayi ya bubbude,sannan ya zauna sosai ya diba duk abubuwan da suka dace,ya shirya saman wani tattausan kilishi zagayayye dake shimfide qasan dakin. "Come" Ya furta a nutse,bata jin zata iya cin komai,amma bata iya musa masa ba,saita taso a nutse yana tsaye yana jiranta har ta iso,idanunsa a kanta da wannan sassanyan takun nata. Ya zaunar da ita sosai saman shimfidar,sannan ya zauna opposite dinta yana saka plate din abincin a tsakaninsu,ya debo da spoon yana dubanta. "Bismillah" Saita girgiza kanta. "Banajin yunwa" Shima kan ya girgiza mata. "Bazai yuwu ba....bakici komai ba tun da safe...." Idanu ta daga ta kalleshi. "Yes....birra ta gayamin" Ya furta yana lumshe mata idanunsa. Stubborn silent dinnan nata ta masa,ya narkar da idanunsa cikin nata yana langabar mata da kai,da wannan soft dangerous patience din nasa yana dubanta. "Are you punishing your self?......" "......or punishing me?". Lips dinta ta cije kadan,ya sanyata taji wani abu da take ganin bai kamata ta jishi ba yanzun. Sake debowa yayi ya miqa mata. "Take one bite" Kauda kanta ta sakeyi,batajin komai zai wuce ta maqoshinta. Shuru ya ratsa tsakani,dubanta yake,tsakanin shi da ita baisan zuciyar waye tafijin zafi ba. "If you collapse too..." Ya fada a tausashe. "......who will stay beside momma....falaak and ahmad?" Nan take idanunta suka sauya. "And you stop eating....." ".…I’ll stay awake all night watching you instead of fixing this.” Ji tayi ya qarasa karyata gaba daya,ba zata iya ci gaba da musa masa ba. A hankali ta buda bakinta kadan,da wani kulawa da taushi ya sanya mata spoon din a bakinta. Ta shiga taunawa a hankali yana binta da wani irin kallo. Calm,protective.....zuciyarsa dauke da wasu sirrika masu nauyin dake son rinjayarsa....💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 112* Wata irin rana ce data kasancewa akhnan da wani irin tsananin da bata taba hasashe ko tunani ba. Wata irin rana da bata taba kawo akwai ranaku masu tsanani a rayuwa kwatankwacin wannan ba. Ranar data bude idanu cikin masarautar.....taga ta kowanne sashe masarautar a rikice take. Komai baya tafiya daidai,idan ta kira hakan da YAQI batayi daidai ba,don komai ma ya faru,yana kuma ci gaba da faruwa. A sannu a sannu masarautar tana fara zama shuru.....wani irin shuru dake nuna janyewa da raguwar mutane daga cikinta. Wasu sun janye a hankali sunbi duhun dare sun sauya muhalli daga masarautar. Saboda tsoro......tsoron kame....tsoron d'auki d'ai d'ai da akebi ana yiwa ahalin masarautar da laifukan da basu taka kara sun karya ba. Laifukan da basu da wani babban dalili da za'a kama kuma a tuhumeka saboda shi. Wasu an koresu haka siddan,an nesantasu da masarautar da shekarun da ba'a qayyade musu yawansu ba da laifukan da basu aikata ba,basu kuma da hujjar kare kansu,basu ma da wannan qarfin iko kona gwiwar da zasuyi defending kan nasu. Ciki kuwa harda nannie shehnaz da a shekaran jiya suka tattara suka bar cikin masarautar. Abinda ta kasa jura a yanzun shine,aisa data shiga sahun wad'anda aka kamesu. "Aisa a prison?" Duk sanda ta tuna wannan sai taji gaba daya kanta ya mata nauyi......wani abu yana juyawa cikin kwanyarta. Abu biyu.....abu guda biyu ne yake bata mamaki gami da d'aure mata kai. Na farko haisam.......basai an gaya mata wayeshi. Ta sani a yanzu a duniya gaba daya ba inda bazaiyi magana aji ba.......amma me yasa ya zabi yayi shuru?,me yasa ya zabi ya zuba idanu ana kame jininta?. Da farko ahmad......yanzu kuma aisa?. Nannie tabar gidan ya sani.......amma me yasa bai dakatar ba?. Sanda sultane yana rage shine wakilinsa,a lokacin......duk da tana jin haushinsa......duk da babu jituwa ko guda daya a tsakaninsu......amma ita kanta tasan ya riqe masarautar sama da yadda sultane ke tafi da ita....ya kuma taka rawar daya dace. Batasan daga gidan daya fito ba a lokacin......amma ta jima tana mamaki. Amma me yasa yanzu yake kauda kai daga dukkan komai?,me yasa a sanda ya dace ya magantu yake yin kamar baisan abinda ke faruwa ba?. Abu na biyu MAMMINA.....wata mace take gani daban.....muguwa azzalumar da zalincinta ya sanya kwanaki biyun nan kanta ke shirin bugawa da tunani. Me yasa ta raineni a baya?.....me yasa ta riqeni har girmana?. Amma a sanda ta soma shigowa da'irar tunani akan girmanta.....aurenta da aka yita yunqurin yi sai wasu abubuwa suka fara kwancewa a kanta. Abubuwan sa suka sanyata zama sosai saman tiles na dakin kamar wata zautacciya tana qoqarin fito da wasu abubuwa,amma koda ta zurfafa tunanin saboda ba wanda zai taimaketa ya tayata fiddosu sai kawai kanta yahau ciwo,a nan ta zame ta kwanta. "Tana da shiri.....akwai abinda taso cimmawa muguwa ce.....ba yadda za'ayi mutumin da bai kasance mugu ba ya sauya dare daya irin wannan" Wannan tunanin ya dunga yamutsa kwanyarta.....har tayi wani wahalallen bacci da yazo mata da mafarkin sultane. Ta manta komai daya gaya mata......amma ta riqe abu biyu zuwa uku. "Shine mamminki.....shine bappi dinki......ba mugu bane" Koda ta waiwaya bayanta.....sai taga haisam ne,a tsaye yana kallonta yana murmushi,data sake juyowa ga sultane kuma sai taga ya bace,take ta farka firgigit. Tana farkawa din kuma haisam din ta samu zaune a gefanta yana karatun qur'ani,ya kalleta da narkakkun idanuwan nan nasa,sannan a hankali ya soma gaya mata abinda ma'aiki yace ayi a sanda kaga wani mafarki daya firgitaka. Ta sake tuna dalilin kama aisa a shekaran jiya. CIN AMANAR SAHEL COUTURE......sahel couture din da batasan a yanzun mallakarta bane ko mallakar mammina?. Ko mallakar wadanda batasan su waye ba da taji sun siyeshi bayan anyi gwanjon kamfanin saboda karairayewa da darajarsa tayi. To wa aka bawa kudin bayan an saida?. Oho.....itama bata sani ba,tunda ba wannan bane yanzun a gabanta ba. "WACECE MAMMINA?" Tambayar da tun a waccan ranar take yawaita yiwa kanta ita kenan.....tambayar kuma data tabbatar akwai tarin amsoshi a qarqashinta. Sahel couture yana da matuqar girma da daraja a idanunta.....amma darajar aisa da shehnaz kawai ya zarta nashi.....ballantana sultane dinta data rasa gaba daya?. Itakam tunda ta rasa sultane kuma akwai wani abu da zata rasa wanda zai gigitata ko ya daga hankalinta?. "Akwai" Taji wani sashe na zuciyarta ya fada mata. "Haisam" Ta sake bata amsa zuciyartata sanda take zaune cikin balcony dinta tana jin yadda masarautar gaba daya take canza mata daga sunan GIDA. Gidan da take matuqar so saboda mutanen dake cikinsa......a yanzun tana jinsa yana koma mata daidai da KURKUKU. "Haisam" Ta fada a hankali can qasan zuciyarta. Haisam.....wata halitta guda daya da a yanzun batasan gwargwdon matsuyinsa a rayuwarta ba. Wani halittar d'a namiji daya tal baya ga sultane da suka samu wani mahaukacin muhalli a zuciyarta. Kamar wata amsa zuciyarta keson bata,saita daga idanunta a hankali haka kawai tanason tantance yanayin da sama take ciki saboda yadda take bada iska me laushin dake qara mata kewar sultane da kuma karyewar zuciya,sai idanunta suka sauka a kanshi. Sanye da baqar Emirati thobe.....kwantaccen baqin gashin nan nasa yayi luf saman kansa yana glowing da ragowar dudashen hasken rana da sama ta barwa duniya. Batasan me tafi so a tattare dashi ba......wannan sexy eyes din nasa?.....ko wannan lips din nasa da yake sanyata mantawa da komai?.....ko kuma idanun nan da take tunanin tun ranar farko data gansu suka fara dulmiyar da ita?. Dulmiyar da batasan tayi ba sai daga baya bayannan?. Ko wannan ginannen jikin nasa?......ko kuma coolness da calmness dinsa?. Mu'amalar nan tasa me taushi?,me tsayawa a rai?.....ko kuma wannan GIRMA da yake bawa diya mace a rayuwarsa gaba daya?. Ko kuma dai yadda bai d'auki kansa a bakin komai ba,bayan yakai ya dauki kansa wanin?. "Gate up" Ya furta a nutse sanda ya iso gabanta. Idanunta ta lumshe tare da budesu gaba daya. Fushi ya kamata tayi dashi,haushinsa ya kamata taji......yaji ya kamata ta masa......amma ta kasa. Duk sanda zai kalleta da wadannan idanun.....duk sanda zai tsaya a gabanta duk sai taji kwarjininsa ya mamayeta. Tana jin yana kakkarya zuciyarta da kallonsa kawai ba tare da yakai ga yin magana ba.....hakanan ta samu kanta da d'ora hannunta cikin nasa sanda ya miqa mata tattausan tafin hannunsa. Bata ankara ba ta jita lullube cikin faffadan qirjin nan nasa.....wannan faffadan qirjin daya zame mata wata mafaka ta samun nutsuwa da duk duniya bata jin akwai wani guri da zata samu shigen wannan nutsuwar. Wannan faddadan qirjin dake cike da tausayi rahama da kuma jin qai. Wannan faffadan qirjin dake cike da hikima yake lullube da jarumar zuciyar da kullum idanunta ke kalla da wani irin alfahari. Ajiyar zuciya taji ya sauke har sau uku,kaman akwai wani abu a boye dake damunsa. Ya lumshe idanunsa yana jin yadda wannan dumin nata dake bashi comfort yake ratsa gabbansa a hankali yana tayar masa da wannan feeling din da yakai wani saqo ya binneshi da zummar adanashi zuwa wani lokaci. Sai daya tabbatar ya aike ma da zuciyarta nutsuwar da zata isheta na awannin,sannan ya janyeta yana motsa wadannan labban nasa da take matuqar so. "Get dressed" Ya fada yana rarraba kallonsa tsakanin blue eyes dinta da suka rame kadan. "Ina zamu?" Ta tambaya tana motsa tiny lips dinta daya gaza jurewa,sai daya matsa da bakinsa yakai musu sumbata kadan. "Zaki gani" Ya fada yana riqe tsintsiyar hannunta softly. Kai tsaye ya bulla da ita bedroom din da suka zabi kwana a ciki tun ranar da suka sauka a agadez din. Yace dai ta shirya,amma ja tayi ta tsaya,tana kallonsa ya bude bangaren daya adana mata kyawawan hijaban da aka dinkasu da wani irin dinki me aji da tsadajjen yadikan da ko sunansu bata sani ba. Ya ciro wani dark coffee ya wareshi,ya sanyata mata,sai ya juyata zuwa fuskar madubi yana daure mata igiyar hijabin,fuskarta da tasa dukka suka bayyana,ya zube mata qwayar idanunsa yana kallon fuskartata yana jin wani abu me qarfi a kanta yana ratsashi,tun daga fatarsa har zuwa jini da b'argonsa. Ya ci gaba da daure igiyar hijabin a hankali kamar wani abu mai daraja da yake tsoron ya b'aci. Itama sai ta kasa d'auke idanunta daga reflection d'insu cikin mirror d'in. Yadda yake tsaye a bayanta… yadda dogayen yatsunsa suke gyara hijabin nata da nutsuwa......komai nasa yana saka zuciyarta bugawa da wani irin nauyi. Daya kammala bai matsa baya,sai yaci gaba da tsaiwa kusa da ita.....ba kusa kawai ba.....wata irin kusa da har jikinsa yana gogar nata,idanunsa cikin nata ta cikin mirror din. "You look dangerous.” Ta d'an had'e gira saboda yadda ya fad'i kalmar cikin low voice d'in nan nasa wadda ta tilasta tsigar jikinta zubawa. Kamar dai zuciyar da gangar jikin sunason mantawa da yanayin da take ciki,kamar dai suna gaya mata MUNA KEWARSA. "Dangerous?" Ta fada da wata murya kamar meyin rad'a. Sai ya d'an sunkuyar da kansa kusa da kunnennata. "Mm" Ya fada yana sauke wani irin nannauyan numfashi. Ya sake maida idanunsa kan fuskarta ta cikin madubin ba tare daya d'aga kansa ba. "Beautiful enough to make a sane man forget himself.” wani abu me sanyi taji yana bin dukka sassan jikinta,sai ta kauda idanunta daga mirror d'in saboda kallon nasa ya fara kassara mata qafafu. "Kana yawan fad'in abubuwan da suke rikita mutum.” wani lallausan murmushi ya saki,qaramin murmushin dake nuna zallar miskilancin dake b'oye a bayan izzarsa. "And you keep doing things that make me say them.” ya fada yana narke mata da wannan sakalcin nasa daya kwana biyu bai gwada mata ba. Lips dinta ta hade dukka ta tura cikin bakinta don tana qoqarin hana kanta yin dariya. Sai ya d'aga hannu ya gyara d'an gashin daya kwanta kusa da goshinta yana maidashi sosai cikin hijabin. Yatsunsa suka d'an shafi fatarta lightly. Idanunsa ya lumshe saboda wani saqo da hakan ya aike gabbansa suna gaya masa kamar kusancin ya masa yawa. "Haisammm" Ta kirashi da wannan sunan.....ta kirashi da wannan yanayin da yake qishirwar ji a tattare da ita "Me yasa kake kallona haka?" Ta tambaya don da gaske yana narkar mata da zuciya ne kawai,a yanayin da takejin duka irin wannan abubuwan dole tayi nisa dasu,don har yanzu tana jin rashin sultane a tattare da ita. Sai ya bud'e idanunsa slowly ya sake had'a su da nata a mirror din da wani irin intensity.💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 113* _________________________ *_SHUWA INCENSE AND MORE_* 😊 *_kai daga jin sunan basai an gaya maka ba_* *_kai daga jin sunan basai ka tambaya ko tsaya tunanin maganar me ake ba_* *_MAGANA CE TA GIDAN QAMSHI_* *BAFA GAMA GARIN QAMSHIN DA KIKA SABA JI BA HAJJAJU* *KINA QONA TURARE YANA QAURI* *KINA SAKA KHUMRA TANA BIN SHANUN SARKI* *WANNAN DIN TURARE NE DAKE DAWWAMA A DAKI DA JIKI.....DA SALON QAMSHIN DAKE MANTAR DA ZUCIYA DUK WANI B'ACIN RAI* *TASTED AND TRUSTED👌👌👌100% HAJJAJU* *NA DABANNE A CIKIN NA DABAN*🙌🏽🙌🏽 *idan akazo kan SHUWA INCENSE an tashi magana* *idan ma kinsan baki shirya jan magana ba a duniyar qamshi to kisha zamanki hajajju* *_zaku iya magana da ita kai tsaye ta wannan number wayar_* +234 704 229 3387 __________________________ "Because every time I look at you…” sai ya sake sassauta muryarsa sosai tana yin can qasa. "..…I feel like Allah spent extra time creating you.” da qyar ta iya qwatar numfashinta ta kuma saukeshi a hankali saboda yadda ya sanya zuciyarta na bugawa da wani irin qarfi. Juyowa yayi da ita a tausashe da wani irin sanyi tana fuskantarsa sosai har suna musayar numfashi. Kallon da yake mata yanzu sanyayar mata da kowacce gaba yakeyi da wani tarin sonshi da qaunarsa. "Sannan.....wannan hijab din....." Ya furta hana mutsuka yatsunsa saman kafadarta da wani irin softness kaman yadda tantance sulb'in yadin. "...…is already testing my patience.” wata irin kunya ce ta taso ta lullubeta,ta kuma fahimci sarai abinda yake nufi.....amma sai takejin zai mata nauyi. A irin wannan lokaci?,a masarautar?. " Haisaammm" Ta kirashi da wannan sound din da wannan yanayin. Sai kawai ya langabar mata da kansa kamar wani innocent man. "What?" Ya fada a narke yana sauke mata murmushi. Boye fuskarta tayi cikin qirjinsa tana jin wani sanyi da sassauci yana saukar mata. Ba shakka MIJI NA GARI duniya ne.....a kowanne rashi da mace zatayi....kowanne irin maraici da zata fuskanta,muddin akwai miji na gari....komai zata fuskanceshi da wani irin sauqi da sassauci. "Muje kiga abinda na kawo" Ya fada yana janyeta daga jikinsa yana saka mata takalmanta. Hannunsa cikin nata.....ba tare da damuwa da mutanen da suke wucewa ba dama me kallonsu. Cike da wannan kulawar da tattalin suke takawa. Yana mata hira kadan kadan da ta sake dauke hankalinta,sai gasu a babbar bargar dawakai na gidan. A nan dawakanta suke.....da dukkan wasu dokuna da sultane keji dasu. Dokuna masu tsadar gaske da wasunsu ma kyauta ce ake bashi daga sarakai na qasashe daban daban. Zuciyarta taso ta karye,amma daya dafa kafadarta ya juyo da ita tana fuskantarsa idanunta cikin nasa sai wani abu ya sassauta daga zuciyarta. "Kin shirya?" Ya tambaya da kulawa. Kai ta gyada masa a nutse duk da yadda zuciyarta ke bugawa kadan kadan,saboda gurin ya tuna mata abubuwa masu yawan gaske game da sultane. Tun daga quruciyarta zuwa girmanta da rabuwarta da gidan dalilin aure. Hannu ya sanya da kansa ya bude mata,saboda cikin gidan sam baya yawo da guards dinsa. Musamman idan har tare yake da ita,tana mamakin yadda yake kaffa kaffa da ita. Suna sanya qafa wata kyakkyawar Arabian mare ta fito(macen doki ingarma na musamman,irin wanda su kansu masu dawakin sunsan na dabanne). Idanu akhnan ta waro waje wani numfashin mamaki yana qwace mata. "Ma sha Allah....tabarakallah" Ta fada da sautin daya sanyashi waiwayawa ya kalleta. Abubuwa da yawa.....dabi'u da yawa nata sun fara sauyawa zuwa na koyarwar musulunci sosai. A baya zata ce wow ko wani abu makamancin haka....amma a yanzun kalaman bakinta sun sauya ba tare data sani ba. Zame hannunta tayi daga nasa tana isa gaban dokin da wani irin d'oki. A hankali tayi d'age saboda tsahon dokin,ta dora hannunta saman wuyanta tana shafawa a hankali. Kamar tasan waye a gabanta sai itama dokin ta sunkuyar da kanta. Hannunsa nade a qirjinsa yana monitoring irin walwala da farincikin daya gani cikin idanunta,wadanda suka bace bat daga randa rasuwar sultane ga shiga kunnenta. Iya wannan kawai ya isheshi nasa farincikin shima. Waiwayowa tayi tana kallonsa. "Ina ka samu irin wannan dokin?" Ta fada da murmushi,saidai bayan maganan ta fito sai taji tambayar ta mata banbarakwai bayan kwanyarta ta dawo mata da hoton WANENE HAISAM din. Da tarin sauqin kan nan nasa sai ya saki murmushi,ya sauke hannuwansa yana takowa cikin nutsuwa inda take tsaye. Hannunsa ya d'ora saman dokin yana tayata shafashi a nutse "You still remember that race?” ya fada yana saka idanunsa a nata. "No" Ta fada a hankali tana dubansa itama da blue eyes dinta dake wani shining ta siririn hasken almurun. Taku uku ya qara,ya kama hannunta suna matsawa daga gefan dokin kadan,ya sanya hannuwansa dukka yana riqe da qugunta suna musayar numfashi a tsakaninsu. "Kin manta?.....You chased me for months after that.” Numfashinta ta riqe a hankali,hippodrome yana dawo mata fes a kanta kamar yanzun komai yake faruwa. Wannan qwararren mahayin daya fara sanya mata tsorom tsere na farko a duniya....boyayyar fuskar nan.....wadannan idanun da su kadai suka bayyana kansu.....sai faduwarta ta farko rashin nasarar farko cikin rayuwarta. "Kaine?" Ta fada da wani irin excitement a fuskarta tana waro idanunta gaba daya waje. "You were the rider at Hippodrome?” ta sake maimaitawa da alamun dake nuna ta dade tana zargi dama. Qasa yayi da kansa kadan,murmushi yana qwace masa. "The one who stole your trophy.” ya fada da wannam ginshirar tasa. Idanu ta zuba masa cikin tuhuma "You let me spend all those years looking for you?!” dariya ce ta subuce masa....karon farko da taji nutsatsen sautin dariyarsa tunda take dashi,sai kuma abun ya mugun qayatar da ita ta sake zuba masa idanu sosai tana kallon yadda yau dariya ba murmushi ba suka masa kyau. "You looked angry enough to stab me if you found me wallahi." Ya amsa mata yana ci gaba da dariyanshi harda dan janye kafadarsa baya kaman da gaske tsoronta yakeji. Hannunta ta dunqule,tadan kaiwa qirjinsa duka tana danne dariyarta data tuna yadda ta zama frustrated sosai a sannan sabodashi.....saboda abinda yayi mata. (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) "Haisammm" Ta kira sunansa kamar me magiyar ya daina mata dariya. Qugunta ya sake kamowa yana matsowa da ita,saita sake dukansa kamar me son turashi baya. "You should’ve seen your face when you lost.” ido ta sake zarowa waje. "I never lose!" "You did that day...." Ya fada cikin salon tsokana yana sake matsowa jikinta. "....to me" Ya qarasa fada da calmness. "Ha'intata kayi....you cheated" Ta fada tana narke idanunta a kansa. "Mm..." Ya fadi yana kulle idanunsa cikin nata. "How?" Ya tambaya da innocent tone. "Ka boye fuskarka ne ai" "....inda kin ganni a wannan ranar gimbiya....." Sai ya dakata da salon sabuwar tsokana. "Definitely you wouldn’t have focused on the race.” sai ta kasa magana. Saboda yadda yake kallonta yanzu,kamar ya san adadin tasirinsa a kanta completely. "The eyes...." "I know those eyes" Ta fada da muryar rad'a. Matsowa ya sakeyi sosai kusa da ita,har tana jin dumin numfashinsa dake fita gauraye da qamshinsa. "Kin gane ni ta idanuwa na?" Ta gyada kai a hankali. "They irritated me first.” "Then they stayed in my head". Wani abu mai qarfi ya wuce cikin idanunsa,sannan ya zarce zuwa zuciyarsa. Tana sake bud'a masa wani rufaffen sirri na zuciyarta.....rufaffen sirrin da ba wanda ya sani a yau....sai yaji tana sake lalata zuciyarsa. "Good" Ya fada yana lumshe idanunsa da budesu. "Good?" Ta tambayeshi tana hade girarta. Murmushi ya sake kubce masa. Ya daga hannu yana shafan gefan fuskarta a tausashe. Ya masa....hakan ya masa,yana sake sanin cewa baiyi kuskure ba da irin zurfin da soyayyarta ya bari ta masa,tun daga ranar farko....tun a ranar datace ta kasa mance idanunsa,shi ya kasa mance komai nata ne....tun daga wancan ranar yake kokawa da komai da zai tuna masa da ita don ya fuskanci aikinsa....ashe qaddararsu tana kulle ne a guri daya. "I hated the thought that another man’s face might stay in your memory longer than mine.” ya furta yana jin tsananin kishinta cakude da matsananciyar soyayyarta suna gware a zuciyarsa. Hannunta ta d'ora saman nasa hannun,tana sake nutsa idanunta cikin nasa,tana sake karantar zurfin son da yake mata. Saidai hayaniya qaqqarfan sauti kuka da haniniyar dawakai ta ratso da katse musu wannan daddadan yanayin. Dukkaninsu suka waiwaya cikin mamaki suna duban daya qofar,sannan a tare suka taka zuwa bangaren. Wani irin yanayi na zallar mamaki ya bayyana saman fuskar Akhnan. Dawakai ake fitarwa.....dawakai kuma na sultane ma ana loda su cikin wata mota da suke hangowa daga can inda suke tsaye. Dawakan sultane masu tsada da daraja.....wasu dawakan ma baya hawansu tsabar sabo kawai ana kiwonsu ne ana kula da lafiyarsu gami da fiddasu lokaci lokaci sdon su motsa jikinsu. "No!" Ta fada da madaukakin sauti ba tare data shirya ba sanda ta hangi mammina na bada umarni gami da magana da ma'aikatan dake fita dasu. "Ku kula da fararen can.....suna da tsada sosai.....wanda yafi biyan kudi me yawa a sallama masa" Maganarta ta kawo har nan inda suke tsaye. Da wani irin shock ta juya tana kallon haisam "Sai dasu take.....dawakan bappi.....abun debe kewarsa" Idanunsa ya lumshe ya kuma budesu lokaci daya yana duban Akhnan din. Yadda yayin sai zuciyarta ta gaya mata bazaiyi komai ba akai ba.....bazai dauki mataki ba,don haka ta qwace hannunta cikin ba zata ta taka zuwa gaban ma'aikatan. "Wadannan dokunan bappi ne....yanason dokunansa!!" Ta fada a tsawace kaman fushin yanason fiddata a saiti. "Ranki ya dade kiyi haquri.....umarni aka bamu na fidda duk wani abu me daraja daga gidan nan a yau dinnan". Sai a sannan mammina ta lura dasu......da wani irin taku me cike da izgili take matsowa gurin. Bata taba jin ta rainashi ba irin yanzu.....ashe damisar kwali ce shi?,kwarjinin daga nesa ne kawai?,zaton duk da take zai zame mata cikas ashe ba haka bane?. Tanadin data masa duk taji yana zuba,na meye ma zata tsiyayar da energy dinta akan wanda bai isa ya dakatar da ita da komai ba?,bayan saura kadan aikinta ya kammala?,saura kadan ta cika dukka burikanta?. Idan wannan dad'adden burin ya cika sai taji dashi daga baya,kwana daya ne tak ta gama dashi. "Kaima kazo ne ka kwashi rabonka ka tarar an rigaka ko?. Allah sarki.....duk da ibraheem nada dukiya sosai ta gasken gaske.....amma banajin d'ansa zaiyi qoshin da abun wani zai gaza burgeshi". Cak maganan ta masa tsaiwar mashi cikin kunnuwansa. " Karka yarda kome zatayi ya tunzuraka inde akaran kanka ne da mu iyayenka.....kome zata furta" Ya tuna maganan motii dashi ta qarshe. Hannunsa ya dunqule da qarfi yana cije haqoransa yana qoqarin controlling kansa. "Mammina!.....kinsan irin kuskuren da kikeyi?.....me kike shirin aikatawa......kayan bappi?....dukiyarsa.....alamar mulkinsa?" Sheqeqe ta kalli akhnan dake magana kaman zata shide. "Kayan mamaci?....me zamuyi da kayan mamaci?,shi kansa qasa yanzun ta fara cin namansa bare abinda ya mallaka.....dole mu share tarihinsa" Ta fada kalmarta ta qarshe tana fita da murya qasa qasa. Yaga meye a idanun akhnan a sannan......yasan kuma makamin da mammina keson amfani dashi kenan ta fiddata daga hayyacinta. Tayi abinda bai dace ba a idanun mutane,don haka taku uku kawai ya isa gaban matarsa,ya kuma kamota ya sanyata cikin jikinsa ya rungume ba tare da shakka ko kunyar kowa ba,ma'aikatan wadanda suka juya da sssarfa suka fice,ko kuma mammina da tayi mutuwar tsaye tana dubansa da wani mahaukacin qiyayya da takejin kamar ta sanya musu wuta a take a gurin. *zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 08187255862 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 08187255862 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 114* ________________________ *_Amintaccen gurin siyayya_* *_ingantattun kaya akan ingantaccen farashin da ba irinsa a kasuwa_* *_BONONZA DA PROMO akai akai_* *dukka sai a HUGUMA CLOSET* *Duniyar kayan yara,mata,maza,dukka* *shaddodi,atamfofi,laces,abayas,jakankuna,takalma,agogo,sarqoqi,English wears,night wears,under wears,da duk wani nau'in sutura babba da qarami* *_Karki yadda ayi babu ke.....leqa kiga yadda closet din HUGUMA kullum ke cike da kaya akan farashi me kama da KYAUTA_* *_YAN SARI....YAN REPOSTING.....DA SARAKAN ADO MASU SIYA DON KANSU....DUKKA INA MUKU MARABA_*🤝🤝🤝🤝 https://chat.whatsapp.com/FrqgC0YmUWP4FPmUzYuLJX __________________________ Cikin kunnuwanta yake rad'a mata wasu abubuwa,wasu irin kalamai masu saukar da wani irin sanyi ga zuciya. Kalaman da suka sassauta mata zuciya ta dinga sauke ajiyar zuciya shi kuma yana sanya yatsunsa yana dauke mata hawayen. "Kina sonsu ne gaba daya?" Ya mata tambayar ba tare data zaci haka daga gareshi ba. Jiqaqqun idanunta ta daga ta kalleshi. "You're buying them back?" Ta fada da dusashiyar murya. Wannan murmushin dake da hatsari yayi. "Would you rather strangers keep pieces of your father?” wani lafiyayyen murmushi ne ya qwace mata,ta riqeshi qam qam cikin jikinta idanunta suna tara sabbin hawaye. Godiya takeson masa amma batasan ta wacce hanya ba.....ta kasa magana gaba daya,sautin mammina ya sake ratsasu. "Da wanne arziqin zaka iya siyan dawakai masu tarin daraja irin wannan?,da albashin kudin bincike?,zamu gani" Saita taka tana daga murya. (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) "Kowanne d'aya inaso a ninka farashinsa ga duk wanda zai siya". Idanu suka hada da akhnan,abinda ya gani a idanunta suka sanya tausayinta ya kusa narkar dashi. Kamar tana tuhumar kanta.....me yasa ta zama uwa a gareta?,kamar tana tambayar kanta ya akayi ta shigo ahalinsu?,kaman kuma tana tuhumar me yasa sultane ya aureta?. Kai ya jinjina mata yana mata wani kyakkyawan riqo,kafin ya dagata cak ya rabata da qasa yana rungumeta a jikinsa. Murya can qasa.....ya kuma kulle idanunta cikin nasa yana hanata kallon kowa ya soma mata wata magana qasa qasa,wadda ta sanyata kwantar da kanta cikin qirjinsa tayi luf. Wani mugun tsaki mammina taja tana binsu da mummunan kallo. Ba abinda zai hanata tsinke wannan igiyar soyayyar. Tasan ibraheem.....kome akace yaronsa zaiyi akan matarsa na sadaukarwa ba zatayi mamaki ba. "Aikin banza.....ka dauka kudin wadannan dokunan kamar kudin siyan littafi ne?". Sautin ya isa kunnensa,amma ya hana akhnan taji da zaqaqan kalaman da yake karanto mata har tana jin duk wani bacin ranta yana kwaranyewa. *zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 08187255862 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 08187255862 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 115* ___________________________ https://chat.whatsapp.com/BkfPzSEDhnsIwyCD8LNGkm?s=cl&p=a&mlu=0 *IDAN KINSAN BA ORDER DIN KAYA ZAKI DINGA SAKAWA BA* *IDAN KINSAN BA BUSINESS KIKE DA NIYYAN YI NA KAWO KAYA DAGA CHINA BA KARKI SHIGA* *_DON ALLAH KARKI BATAWA KANKI LOKACI_* *_Assalamu alaikum my loyal people_* *_Barkanmu da wannan lokaci,kuma barkanmu da warhaka_* *_akwai da dama cikin mata wadanda suke sha'awar yin order kaya daga CHINA zuwa NIGERIA,NIJER,CAMERON,CHAD da GHANA_* *_Amma rashin samun amintaccen company....ko hannun wanda zasu dinga siyan kaya ta hannunsu cikin aminci ya hanasu_* *_To a yau addu'ar da yawa daga cikinku ta amsu,don nayo muku tsarabar kamfanin da zakuyi siyayya ta hannunsu su kuma dora muku kayanku har qasarku cikin aminci ba tare da fargaba ko d'ar d'ar ba_* *_kunsan komai nawa TASTED AND TRUSTED ne,to wannan kamfanin idan akwai abinda yafi TASTED AND TRUSTED ma shine_* *_Baki da fargaba kota sisin kwabo,ni SAFIYYA HUGUMA na tabbatar da hakan_* *_Zaki iya kasancewa dasu group nasu,inda a nan zaki hadu da agent dinsu da CEO nasu gaba daya ta wannan link din,zaki samu bayanansu da komai da ya shafi mu'amala dasu_* *INA ME BAKU TABBACIN AMINCI DA INGANCI DA SAUQIN MU'AMALA DASU DA IZININ ALLAH,BAN TALLATA MUKU SU BA SAI DANA GWADA* *Allah ya dafa mana,yasa mana albarka a nemanmu,ya albarkaci halal dinmu ameen summa amee* ________________________ Cikin kunnuwanta yake rad'a mata wasu abubuwa,wasu irin kalamai masu saukar da wani irin sanyi ga zuciya. Kalaman da suka sassauta mata zuciya ta dinga sauke ajiyar zuciya shi kuma yana sanya yatsunsa yana dauke mata hawayen. "Kina sonsu ne gaba daya?" Ya mata tambayar ba tare data zaci haka daga gareshi ba. Jiqaqqun idanunta ta daga ta kalleshi. "You're buying them back?" Ta fada da dusashiyar murya. Wannan murmushin dake da hatsari yayi. "Would you rather strangers keep pieces of your father?” wani lafiyayyen murmushi ne ya qwace mata,ta riqeshi qam qam cikin jikinta idanunta suna tara sabbin hawaye. Godiya takeson masa amma batasan ta wacce hanya ba.....ta kasa magana gaba daya,sautin mammina ya sake ratsasu. "Da wanne arziqin zaka iya siyan dawakai masu tarin daraja irin wannan?,da albashin kudin bincike?,zamu gani" Saita taka tana daga murya. "Kowanne d'aya inaso a ninka farashinsa ga duk wanda zai siya". Idanu suka hada da akhnan,abinda ya gani a idanunta suka sanya tausayinta ya kusa narkar dashi. Kamar tana tuhumar kanta.....me yasa ta zama uwa a gareta?,kamar tana tambayar kanta ya akayi ta shigo ahalinsu?,kaman kuma tana tuhumar me yasa sultane ya aureta?. Kai ya jinjina mata yana mata wani kyakkyawan riqo,kafin ya dagata cak ya rabata da qasa yana rungumeta a jikinsa. Murya can qasa.....ya kuma kulle idanunta cikin nasa yana hanata kallon kowa ya soma mata wata magana qasa qasa,wadda ta sanyata kwantar da kanta cikin qirjinsa tayi luf. Wani mugun tsaki mammina taja tana binsu da mummunan kallo. Ba abinda zai hanata tsinke wannan igiyar soyayyar. Tasan ibraheem.....kome akace yaronsa zaiyi akan matarsa na sadaukarwa ba zatayi mamaki ba. "Aikin banza.....ka dauka kudin wadannan dokunan kamar kudin siyan littafi ne?". Sautin ya isa kunnensa,amma ya hana akhnan taji da zaqaqan kalaman da yake karanto mata har tana jin duk wani bacin ranta yana kwaranyewa. ★★★ A cikin kwanaki kad'an ta soma wargaza masarautar da tarin sauye sauye na fili dana boye. Kadarorin sultane......tsarukansa da komai nasa ya zama a hannunta da sarrafawarta. Cikin wani irin qwarewa da take tunanin tana da ita....cikin qwarewar da take ganin ta kai mata take karban komai d'aya bayan d'aya. Manyan kadarorin sultane tana gwanjonsu cikin kwanciyar hankali da yaqinin ba wanda yake da kaurin wuyan qalubalantarta. Dawakan da yafiso....,manyan muqullai suna hannunta,takardu masu daraja....zinare......azurfa.....dama dukkan wani abu da tasan me kima ne. Babu me qoqarin yayi magana.....saboda abune me sauqi yanzun nan ace an rasa wane....ko an koreshi kwata kwata daga agadez din. Mutane da yawa ta siya.....kama daga mañyan fada da jami'an tsaro na cikin garin,wannan ya sake bata daman sakewa da ci gaba da aiwatar da komai yadda takeso. Masu tsaro da amintattun da suka fara canza bangare. Wasu saboda tsoro.....wasu saboda kwadayi da neman mafita irin ta son zuciya da butulcewa halacci irin na d'an adam. A cikin kwanaki kad'an…..masarautar Agadez ta fara sauyawa zuwa wani abu daban da mutane da yawa basu tab'a tunanin zasu gani ba. Ba kuma saboda an rasa sultane kawai ba...aah. saboda mutanen da suka dad'e suna fakewa da inuwa da tsoronsa… sun fara fitowa fili. Fadar agadez ta fara rasa tsohon numfashinta na asali,dokokin da sultane ya kafa shekaru masu yawa an rushe wasu,an sauya wasu. Sabbin fuska suka fara bayyana cikin fadar.....sabbin umarni da sabbin tsare tsare da sabbin dokoki. Komai yana sauyawa cikin sauri me ban tsoro da d'aure kai. Mutum daya.....mace daya data zame mata qarfen qafa.....macen dake tsaye wajen qalubalantarta da dukka tsarinta MORSA SAFIYYA sai lafiyarta ta fara rauni,wannan ya sanya hairaan yanke shawarar hanata jin komai. Ba morsa SAFIYYA kadai ba.....harda akhnan dinma da falaak da suke kyautata zaton laulayi takeyi. Don sam taqi yarda taje asibiti bare a gwadata. Morsa SAFIYYA tayi tayi kuma tabi mijinta su wuce tunda anyi bakwai.....amma tace sai anyi arba'in tukunna. A hankali tsoro ya shiga zuciyar kowa,tsakanin masu aiki sam ba sakewa.....babu aminci saboda kowa ji yake bai tsira ba. Cikin kowanne second....cikin kowanne minti kowa yana iya shiga TARKO na giwa mammina. Uwa uba a yanzun ba kowa ke yarda da kowa ba cikin masarautar. Kana zaune da mutum yanzu,anjima zaka tsinceshi ya koma dan bayan mammina dari bisa dari. Masarautar ta fara zama wajen zargi,tsoro da siyasa,da kuma murmushi na jabu,murmushin da zai iya hallaka wanda ya rud'u da ganinsa saman fuskar mammina din. Sauyi ne daya fara tun daga manyan corridors har dakunan masu aiki na gidan,bayi dama hadimai. Anajin wannan sauyin. Ana ganinsa. Kuma kowa na tsoronsa. Tutar masarautar tana nan a tsaye.....masu tsaro suna tsaye a bakin dukkanin qofofin.....dattawa suna nan a majalisar zartarwa ta fadar agadez,amma RUHINTA ya fara canzawa. A hankali sunan SULTANE ya fara zama kamar wani abu da ake qoqarin turawa baya. Aka fara cire manyan hotunansa daga dogayen private halls na gidan. Ambatar sunan SAFEENA ko 'DA SULTANE YA RAYE' ya fara zama babban zunubin da ba za'a gafartawa wanda ya aikatashi ba. Kalmomi suka fara zama abubuwa masu hatsari cikin masarautar AGADEZ. A hankali akhnan ta fara jin kamar tana kallon gidansu yana zubewa a idanunta. Mammina ta fara zagayawa cikin fada da wani irin nutsuwa da jin gamsuwar nasara ta tabbata a hannunta!.....nasara a hannunta tayi nisan da ba wanda zai iga qalubalantarta. Ba gudu take yi ba....Ba rikici kawai take tayarwa ba. A’a. Ta fi amfani da: umarni masu laushi......murmushin karya,dokoki,tsoratarwa.....da kuma rashin tabbas data saka a zukatan kowa da rayuwarsa. Wani lokaci zata yi magana cikin taushin murya…..amma bayan awa guda wani hadimai ko bawa ya rasa aikinsa. Ko wani cikin masu tsaro ya b'ace. A hankali sai mutane suka fara fahimtar mulkinnan na mammina......sannan mulkin mammina ba ihu bane. Mulkin Mammina… shi ne ka kwanta lafiya,ka tashi ka tarar an canza rayuwarka. (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) Jama’ar Agadez sun fara shiga rud'ani. Wasu suna kuka da gaske saboda rashin Sultane. Wasu suna tsoron future ɗin masarautar. Amma kuma.....ba wanda ya isa ya fada da qarfi. Fadar agadez ta fara zama wajen sirruka. Qananan qungiyoyi suna had'uwa cikin boyewa. Ana kai takardu cikin duhu. Ana canza masu gadi a tsakar dare. Ana jin jita-jita marasa dad'in ji kala mala. Wasu daga cikin tsoffin masu biyayya ga sultane sun fara ja da baya cikin tsoro. Saboda sun kasa gane.....wa za’a yarda dashi?......wa yake siyar da bayanai.......wa zai biyo bayanka idan kayi kuskure???. Duk sanda wani zai magana amsa daya ce. "Ina tattalin masarauta.....ina tattalin mutuncinta.....ba abinda zai sake gudanawa sai an tabbatar da wanda ya kashe sultane.....sai bayan bincike ya kammala tare da kama duk wanda ke da hannu cikin mutuwarsa". Wanda yayi wannan maganar har ya samu amsa.....ba lallai bane gobe a sakejin motsinsa ko a sake ganinsa ba. Wannan ya zama wani abun tsoro da kowa ke shakkar magantuwa akai. A wannan lokacin ne akhnan ta fara jin cewa.....ba fadarsu bace wannan kwata kwata.... Ba masarautar mahaifinta bace......duk inda ta juya sai ta ga canji Wani sabon tsari. Wani sabon umarni. Wani sabon tsoro a idanun kowa. Sai dai abu d'aya bai sauya ba. Kallon Haisam!. Duk lokacin da idanunta suka had'u da nasa.....tana jin kamar. Akwai wani abu daya sani da kowa bai sani ba!. Kuma wannan abu… shi ne kad'ai yake hana masarautar rushewa gaba ɗaya. *HAISAM* mutum d'ayan da ya ci gaba da kasancewa cikin nutsuwa mai tada hankali da sanya mamaki. Haisam....yana gani.....yana sani. Amma bai hana komai ba. A kallo… ba a fili ba......a filin kuma KAWAI bawai a bad'ininsa ba. Badinin da ba wanda ya sani sai Allah saishi.....sai team dinsa dake qoqarin tattara dukka wata hujja data motsin mammina!. Wannan shurun nasa......wannan nutsuwar tasa....shine ya fi tsoratar da wasu daga cikin dattawan fada. Saboda sun kasa gane?......shin yana jiran komai ya rushe ne?......ko kuwa yana jiran wani lokaci ne da zai maida komai hannu d'aya?. Mammina naci gaba da jin d'and'anon nasara. Karo na farko cikin shekaru,ta fara tafiya cikin masarautar kamar ita ce ke da ikon qarshe a duniya gaba daya. Ba tare da idon sultane a kanta ba.......Ba tare da wani dake iya tsayar da ita ba. Ko a zuciyarta da a farko take shakka da kokwanto......ta fara gaskata cewa...... A iya yanzu kadai TACI YAQIN DATA SHEKARA DA SHEKARU TANA JIRA!!!. ★★★ Babban zauren majalisar masarautar Agadez cike yake da manyan mutane,dattawa da masu riqe da dokokin fada. Masu kula da kadarorin masarauta. Hakimai da manyan masu fada aji. Zaman an yishi ne don a tattauna rabon gadon Sultane,karo na farko tun bayan mutuwarsa,ganin yadda kwanaki ke dada nisa. Cikin manyan malamai aka samu wani ya fidda tsoro ya kuma shirya zaman saboda qaunar da yakewa sultane din da kuma fatan sauke masa nauyi koda hakan zai zama silar faruwar wani abu a kanshi. Wurin ya yi shiru mai nauyi,irin shirun da yake nuna kowa na taka-tsantsan da kalamansa,sannan kowa na kallon kowa da zargi da rashin aminci. Mammina na zaune cikin baqar alkyabba mai nuna iko da isa. Fuskarta babu alamar wata damuwa irin ta macen data rasa mijinta masoyinta kuma jigonta. A gefe guda kuma morsa safiyya ce,zaune cikin nutsuwa duk da alhini da gajiyar da suka bayyana a idanunta dama gangar jikinta data nuna rama sosai. Kusa da ita kuma akhnan ce zaune,tashin hankali ne kwance saman Fuskarta yana nuna kansa muraran. Tun bayan mutuwar sultane ta fara jin kamar masarautar tana zamewa daga hannunsu. Tun biyowar bayan sabon takun mammina da har yanxu yake daure mata kai takejin komai yana dagulewa cikin rayuwarta. A can gefe kuwa haisam ne,yana zaune shiru. Cikin wannan tarin nutsuwar tasa,haiba cikar kamala,yana kallon komai cikin idanun da basa bari a gane me ke zuciyarsa. Baiso zuwa zaman ba.....amma takanas morsa safiyya ta sameshi da roqon alfarmar ya shiga zaman. "Kai kadai muke kalla yanzu a matsayin wakilin sultane da muka yarda dashi" Ta fada muryarta tana rawa. Magananta da yanayinta yaso karya masa zuciya. Yanajin kamar ya bayyana mata nanay ko zata samu sassauci daga radadin da takeji. "Zanje.....zanje in sha Allah" Ya amsa mata. D'aya daga cikin dattawan majalisa ya gyara zamansa kafin yayi magana ta farko tun bayan zamansa a gurin. “Kamar yadda dokokin masarauta suka tanada…” ya fada yana bud'e wasu takardu “…akwai kadarorin da baza’a tab'a ba har sai an tabbatar da sabon tsarin mulki.” bata ko d'aga qafa ba mammina ta d'ago kai da sauri. Mamaki take......dama akwai wanda ya rage da zai qalubalanci abinda ta tsara tana so?. Duk da komai yana hannunta,abinda yayi saura baida yawa.....Shima tana da interest a kansa gaba daya. Don har yanzu wannan ZUCIYAR DUKIYAR AJANI din da take kyautata zaton na hannun sultane iya bincike bata ganta ba. *zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 08187255862 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 08187255862 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽 💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 116* _________________________ *_Mg's ORGANIC SOAP_* *_Shin kin gaji da banke banken sabulu wa fatarki?_* *_Kullum ba ci gaba?_* *_Kullum jiya iyau sai sake lalacewa ma da takeyi?_* *_matso maza ga maganin matsalanki da izinin Allah_* *MG'S ORGANIC SOAPS* *_kamfanin da ya shirya tsaf don samar miki da sabulun da zai sanya fatarki KYAU ta goge tayi haske ME AJI bana bleaching ko me bata fata ba_* *_KALAN 'YAN ABUJA.....kalar hutu hajjaju,asalin kalar fatarki ta anihin_* *_Masu matsalan SKIN irinsu PIMPLES,SPOT,ACNE,SUNBURN in sha Allah kukanku ya qare....matsalarku ta qare_* *AKWAI PACKAGE DA SUKE HADAWA GAME BUQATA* *yammata.....zaurawa....amare.....da iyayen gida masu capacity wanda ya hada da* Soap Facewash Face cream/body cream Scrub Serum Cleanser Glow oil Toner *duka cikin package din* *_INA MASU FAMA DA NANKARWA(STRETCH MARK)MG'S ORGANIC SOAP bata barku a baya ba_* *Ku nememu kai tsaye a wannan number don GYARA DA MAGANCE MATSALOLIN FATARKU* 0806 299 1549 *MG'S ORGANIC SOAPS* *_takenmu (MAIDA TSOHUWA YARINYA....A SABUNTA YARINYA ZUWA SABUWAR HALITTA)_* _________________________ “Sabon tsarin mulki?” ta tambaya da gadara cikin muryarta. “Mijina ya riga daya rasu......” “.....Dukiyarsa mallakin gidan sarauta ce.” Safiyya ta amsa cikin nutsuwa jarumta da rashin tsoro. “Kuma gidan sarautar yana da magada." Ta qarasa maganan tana sauke idanunta akan mammina. Wurin ya d'an kaure da maganganu qasa qasa. Wasu suka fara kallon juna. Mammina ta d'an matse lips d'inta,tana jin wannan qasqancin da takeji cikin jininta a duk sanda safiyya ta qalubalanceta,a magana ko a aiki ko a ra'ayi,tun sultane yana raye. “Magaji yana prison.” “Ko ba haka ba?” mammina ta fada tana sanya idanunta cikin na safiyya da nufin bar mata wani ciwo. Da sauri cikin fushi akhnan ta d'aga kanta tana duban idanun mammina. “Ke kika shirya masa!” ta samu kanta da fad'a ba tare da wata shakka ba. Hayaniya ta tashi cikin hall d'in,cikin mamakin qarfin halin akhnan din,wasu amsarta itace daidai da ra'yinsu tuntuni,amma basu da 'yancin bayyanawa. Juyawa mammina tayi kanta a hankali zuwa ga akhnan “Ki kula da harshenki Akhnan.” ta fada cikin sanyin murya mai razanarwa “Rashin ubanki bai kamata ya koya miki rashin hankali ba.” Kafin Akhnan ta sake magana,qofar hall d'in ta bud'e da sauri. D'aya daga cikin jami'an da aka zube cikin gidan tun rasuwar sultane wanda ba wanda yasan amfanin me suke ya shigo. Sai wani jami’in ya shigo da numfashi sama-sama kamar wanda yaci gudu. A hannunsa akwai wasu takardu masu hatimin masarautar agadez. “An samu wasu sabbin hujjoji.” Wurin ya yi tsit nan take maganansa na amsa kuwwa cikin hall din. Idanu haisan ya aza a kanta yana tattara dukka attention dinsa a kannata,mammina ta d'an jingina bayanta jikin kujera. "Calm....too calm" Ya fada can qasan ransa. Jami’in ya qarasa gaban majalisar ya bud'e takardun. “Wasiku ne…” muryarsa cike da nauyi ya dora “…da suka shafi wani shiri na tayar da tawaye.”Jami’in ya ci gaba da karantawa. Lissafowa ya fara yi,sunayen guards,lokutan ganawa da kuma sirrin shirin fasa prison d'in da Ahmad yake kulle. Komai a tsare daki daki. Sai ya karanta layi na ƙarshe. “zuzzurfan bincike ya bayyana cewa dukkan umarnin sun fito ne daga MORSA SAFIYYA". Maganar tazo da wata irin razani.....wani irin gigitaccen yanayi da hankali bai taba kawoshi ba. Wurin ya hargitse da surutai. Wasu suka mikewa tsaye cikin mamaki. “QARYA NE!” falaak ta fada da wani razanannen sauti. Bata gane komai akhnan,kawai hannunta ta miqa gurin da jami'in dake daura da ita yake tsaye ta fizgi takardun daga hannunsa. Da sauri ta fara dubawa,zuciyarta na bugawa. Tunaninta taji kaman zai juye lokaci guda,saboda hujjojin sun yi kama da gaske sosai. “No…” ta fada da harshen faransanci a razane. Cikin rawar murya ta sake cewa “Wannan ba gaskiya bane…” Mammina ta miqe tsaye a hankali,wani kwantaccen murmushi da ba kowa zai iya ganeshi ba kwance qasan Fuskarta “Hajiya Safiyya…” ta fada cikin izgili da cikin cikakken iko “Bisa dokar masarauta…” “…ana zarginki da had'a baki wajen tayar da tawaye akan karbar karagar mulki" "Ina jami'an tsaro?" Ta fada da muryar gaggawa. Kaman a shirye suke daman,umarnin kawai suke jira,nan take suka shigo cikin hall d'in. Makamai d'aure a jikinsu,kamar wadanda sukayi shirin shiga fagen yaqi. Da sassarfa akhnan ta miqe tana matsawa gaban morsa safiyya. Wani irin tashin hankali.....burin bata kariya da bata taba jinsa ba na har abada ya taso mata. “Babu wanda zai taba ta!” ta fada tana fidda manyan blue eyes dinta waje. Dakatawa sukayi,kaman sunji umarni daga gareta ne,saidai ba haka ba. Har yanzu ita din d'iyar sultane ce,wani abu bai sauya wannan matsayin nata ba,kuma ita din matar sheikh haisam ce,babu wanda zaiyi kuskuren kaudata koda giyar wake yasha. Mammina ta lura da hakan,sai idanunta suka qanqance. Wai me yasa har yanzu da sauran wannan mutucin nasu a idanun mutane?,harda mutanenta ma ballantana nasu mutanen?. “Wannan rainin hankalin ne ya lalata wannan gida!” ta fada tana duban kowa dake gurin. "Tana ganin ta isa ta sauya doka kota hana zartar da ita?." Ta fada da sigar tambaya me cike da zafi. A hankali,kuma cike da tarin nutsuwar nan morsa safiyya ta miqe tsaye. Cikin alhini. Cikin mutunci. Kamar ba ita aka karantowa wadannan munanan zarge zargen ba,ta gyara mayafinta cikin nutsuwa,sai ta kalli Mammina kai tsaye. “Ina miki jaje.....Kin kasa cin galabata yana raye.” “Shi yasa kika jira mutuwarsa......wannan itace CIKAKKIYAR FADUWARKI....WANNAN KE NUNA KIN KASA KIN GAZA....ina sake jajanta miki akan gazawarki" ta qara fada wani murmushi yana fita daga saman labbanta. Wannan murmushin dai.....wannan murmushin data tsana a fuskar safiyya. Wai sai yaushe?,sai yaushe zata samu nasarar dakushe wannan murmushin?. ta d'an matse hab'arta tana jin murmushin safiyya kamar zubar garwashin wuta saman fuskarta. “Ku tafi da ita.....doka ta hau kanta” matsawa sukayi,saidai kowa ya kasa saka mata qarfe ko tabata. "Muna iya tafiya" D'aya daga cikinsu ya fada muryarsa da nauyi sosai. (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) Kuka falaak ta rushe dashi,yayin da Akhnan jikinta ya dauki rawa da wani matsanancin fushi. Gaba daya hall d'in ya rikice da wani yanayi me taba zuciya. Duban akhnan morsa safiyya tayi,sannan ta kama hannunta a tausashe tana murzawa da wani yanayi daya taimaka wajen tattara nutsuwarta na dan lokaci. “Ba kowanne yaqi ake cinshi da ihu ba.” cikin nutsuwa ta d'ora “Wani lokacin gaskiya tana jira ne kawai......tana jiran lokaci ta bayyana kanta tayi yado da yabanyar da kowa zai ganta". Saita zame hannunta daga cikin na akhnan din ta fara takawa cikin nutsuwarta. Dab da haisam ta dakata,ta tsaya ta kalleshi still da murmushi. "Ga amanar 'ya'ya na nan.....ina da tabbaci da yaqini a kanka,na yarda dakai d'ari bisa d'ari,ba zaka taba cin amanar sultane ba.....ba zaka gaza daga riqon amanarsa ba.....ba kuma zaka kasa ba har abada" Ba tare data sake kallonsa kota sake cewa komai ba,taci gaba da takawa tana fita,jami'an tsaro a gabanta wasu a bayanta. Kallo daya kawai. Amma kallon ya isa ya saka wasu daga cikin dattawan majalisar jin tsoro. Saboda har yanzu Haisam bai motsa ba. Bai hana komai ba. Kuma wannan shiru nasa… shi ne mafi tayar da hankali a cikin duka masarautar. Baga mammina kawai ba.....ga kowa da kowa,kowan din da ajin da yake sanyashi. "Sun hada kai ne da mammina" "Shima tsoro yake" "Bazai iya da ita ba" Da sauran maganganu masu kama da wannan. *BAYAN SHUDEWAR WASU AWANNI* Daren Agadez ya yi nauyi da tashin hankali mara misaltuwa a zukata da rayukan al'ummar masarautar dama na wajen masarautar. Tun bayan tafiya da morsa safiyya sam akhnan ta kasa samun nutsuwa. Tayi kuka irin kukan daya ninka wanda tayi randa ta tako agadez ta tarar ba sultane babu dalilinsa. Komai yana mata yawo a kai,kama Ahmad,canjawar masarautar da wani mummunan yanayi mara dadin ji ko saurara. MAMMINA......yadda komai ya sauya cikin d'an lokaci. Yadda komai ya fara ta hannunta?. Komai ya soma ta sanadinta?. Komai ita ta shukashi?,ita ta farar dashi?. Ta kasa yarda d'ari bisa d'ari akan haka kawai komai ke tafiya haka,saboda a duk rayuwarta,ko da Mammina tana da tsauri… ta tab'a d'aukarta a matsayin uwa......da idanu irin na uwa take kallonta. Ita ta raineta tun shekarun quruciya har ta girma ta zama mutum......ita ta koya mata abubuwa masu tarin yawa. Ita ta rungumeta lokacin da tana qarama,lokacin da batasan komai ba,batasan kowa ba,lokacin da batasan hagunta ba batasan damanta ba. Ko da akwai nisa a tsakaninsu wannan nisan baya hana mammina sanyata ta jita kamar tana a gabanta. "Amma me yasa?,me ya sauyata?,me ya birkitata ta zama cikakkiyar maqiyiya kuma abokiyar gabar sultane iyalinsa dama masarautar agadez gaba daya?" Ta yiwa falaak tambayar wadda ke kwance a gabanta saboda jirin daya kusa kayar da ita Da idanu kawai take kallon Akhnan,tana jin zuciyarta tana bushewa. Sai yau idanun Akhnan suka fara budewa tarwai kenan take kallon ainihin siffa da kamannin matar?,abinda yake yawo kenan cikin kan falaak wadda kanta ke kwance saman cinyar hairaan dake share hawaye tun dazun ta kasa ma magana. A fusace ta miqe,ta gaji,tana buqatar yiwa mammina wadannan tambayoyin kai tsaye. Tana buqatar ganinta ido da ido,taji meye manufarta......meye matsayarta?,meye dalilinta na hargitsawa da dagula duk wani abu me kyau da sultane ya bari. Tarihi....Kyakkyawan mulki da kyakkyawar mu'amala. Basu dakatar da ita ba.....hakanan kan hanya ba wanda ya dakatar da ita. Har haisam dake takowa zuwa bangarensu don bai shigo ba tun sanda zaman ya tashi,shima baga ganshi ba,idanunta ya riga ya rufe. Shima bai tsaidata ba,duk da baisan inda ta nufa ba,sai da yaga tana dosar shiyyar private chamber d'in Mammina. Da idanu yakewa guard din dake hanya umarni,haka suka dinga matsa mata salin alin ba tare da cikas ko kallonta ba. Guard's din da mammina din ke ganin ta gama mallakarsu da dukka ayyukansu. Qofar ta bud'e da qarfi. Mammina dake zaune cikin nutsuwa da annashuwa da wani golden cup a hannunta ta daga idanunta tana kallon Akhnan din,ba tare data motsa ba.....saidai can qasan ranta tana tambayar kanta abinda ya kawo yarinyar. Ba ita take tsammanin gani ba.....haisam taketa lissafin sanda zai tattaki ya sameta don nemawa mutanensa sassauci. *zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 08187255862 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 08187255862 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 117* __________________________ ✨ AMINTACCEN GURIN SIYAN THRIFT ABAYAS ✨ Ingantattun Thrift Abayas masu kyau da tsari akan farashi mai sauƙi da araha. Muna kawo sababbin kaya akai-akai tare da rangwame na musamman. 🤍 Dukka sai a MK ABAYA BOUTIQUE 🤍 Duniyar Thrift Abayas masu kyau, masu tsari, da salo iri-iri domin kowane lokaci da kowane irin event. Abayas masu inganci, masu salo, masu araha, kuma na zamani ga mata masu son ƙawata kamanninsu cikin kamala da kamun kai. Karki bari a ba ki labari... Leƙo ki ga yadda MK ABAYA BOUTIQUE kullum ke cike da kyawawan Thrift Abayas akan farashi mai kama da kyauta. 'YAN SARI, 'YAN REPOSTING, DA MASU SIYA DON AMFANIN KANSU... DUKA INA MUKU MARABA! 🤝🤍 📱 WhatsApp: 07064399623 📞 Call: 08036027448 🔗 Join our Wholesalers Group: https://chat.whatsapp.com/JBg80RmA47v7GoqvWdgLJT?s=cl&p=a&mlu=3 _________________________ “Me yasa?!” ta jefawa mammina tambayar tana kallon qwayar idanunta da wani irin zuzzurfan kallo da bata taba ganin irinsa cikin idanun Akhnan din ba. “MEYASA kike mana haka?!” sai mammina ta d'ago idanunta a hankali. “Ki rage murya.” ta fada cikin nuna isa da taqama. “morsa safiyya fa?,me ta miki?" hawaye suka gangaro mata. “Ahmad fa?,shima me ya miki?" Ta fadi tana samun tabbacin akwai dalilinta na shirya musu haka. Takawa ta sakeyi,ta qarasa kusa da ita tana jin zuciyarta tana tsatstsagewar,fushi da kokwanto suna rinjayarta. “Ke ce kika raineni…” sai muryarta ta fara karyewa. “Ke ce kika bani kulawa…” “Me ya sauya yanzu?!” Shuruuuuuu......mammina ta zuba mata ido na wasu seconds. Sannan ta saki dariya. Not warm laughter. Wata baqar dariya da tayi qaramar amsa kuwwa cikin dakin,wata dariya data kusa fasa zuciya da kwanyar Akhnan. Akhnan din ta tsaya cak,saboda bata tab'a jin dariya haka daga gareta ba. “Sauyawa?” ta jefawa Akhnan tambayar,tana mata wani qasqantaccen kallo still dariyarta kuma bata tsaya ba. “Akhnan…” ta kira sunanta,sai ta ajiye cup d'in hannunta a hankali. “Kin rayu cikin qarya ne shekaru da yawa.” ta fada idanunta kai tsaye cikin nata tana zurfafa kallonta a kanta. “…Me?” Akhnan ta fada tana jin tunaninta yana girgiza. Miqewa mammina tayi a hankali,ta qaraso kusa da ita. Idanunta cike da wani irin tsohon qunci......kwadayin d'aukar fansa da tsumammen rashin imani. “Kin tab'a tambayar kanki…” sai tayi qasa da muryarta. “…me yasa na d'auke ki bayan mutuwar uwarki?”. Da Akhnan zata iya tabbas data girgiza mata kai alamun aah.....amma saita zabi ci gaba da kallonta kawai. "Banyi saboda Allah ba.....saboda ni ban iya abu bati siddan ba....ban kuma iya abu na jira Allah ya biyani ba,nafi ganewa duka d'auka,nayi a take.....na samu sakamakon alfanun a take" Sai ta dakata tana sauke numfashi. “sannan banyi ba saboda wani INA SONKI BA.....ban taba sonki ba Akhnan,koda na qasa da second daya!" Akhnan ta ji wani abu ya tsaya mata a qirji da wani irin nauyi kaman tana shirin faduwa,har sai data dafe wani table. “…Mammina?” ta kira sunanta muryarta na fita da qyar tana rawa kaman mejin sanyi. Sai Mammina ta matso kusa sosai. “Na raineki ne…” ta fada idanunta suna sake qanqancewa da wani irin duhu. “…saboda in tunasar da ita ta taba qwace a duniya......saboda a sanda take kwance a kabarinta ta tuna akwai wadda ta taba qwacewa abu duniya.....na raineki ne don na dauki fansa.....na aura miki dan uwanki almaz.....ahmad a yanzu bayan na saceshi da quruciyarsa.......na raineki ne don ko sanda tana ramin kabarinta kada ta huta......ko sanda tana ramin kabarinta ta d'an d'ani baqincikin da bazata iya tarewa 'ya'yanta ba......shi yasa na raineki da qiyayayar safiyya,don kada ta zama silar tsiranki” ta dakata tana maida numfashi. Wadannan maganganun data dade da binnesu tana binta da murmushin fake qauna,tana jin a yau ta shirya furzar mata dasu kafin takai rayuwarta mahallaka. Kamar zararriya haka akhnan ta zaro ido,tana jin kamar kowacce gaba dake jikinta ba'a jikin nata take ba. Tana jin kamar hauka ta fara kwanyarta ta samu damuwa shi yasa take rattabo mata wadannan bayanan. “Uwarki.” ta fada da d'aci sosai a muryarta da bai boyu ba “itace mace ta farko da wasu 'ya'ya maza har biyu suka sota kafin ni......ajani.....sannan kuma sultane.....ita kadai ta kafamin wannan tarihin da har na mutu bazai goge ba!." Wani irin sanyi ya ratsa Akhnan. Qafafuwanta suka kasa motsi tana fatan wani ya tasheta a wannan mafarkin. "Guraben da nake muradin mallaka......ita ta qwacesu ta mallakesu.” ta fada da muryar dake nuna tsohon ciwo.....tsohon miki ya tashi. (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) “ta bashi 'ya'ya......ba d'aya ba.....ba biyu ba kafin na bashi koda rabin mutum....ke koda b'ari ne......sannan safiyya tazo ta sake laftamin wani ciwon ta hanyar bashi falaak?.” Akhnan ta soma girgiza kai,wasu iri hawaye da basu da misali.....hawayen da baka isa kayi controlling d'insu ba suka soma mata ambaliya. “A'ah…” ta fada tana girgiza kai,tana jin kanta bazai d'auki wannan abun ba,kamar zaiyi tsawa. "Eh!" Mammina ta fada da qarfi ta yadda zai isa kunnuwanta da kyau. Burinta ta qara hargitsewa ta yadda hakan zai sanadin haukacewarta gaba daya “NA TSANETA!.” Sai ta sunkuyar da kanta kusa da Akhnan. “lokacin data mutu…” “ban so mata mutuwa ba a sannan......naso ta qare rayuwarta tana raye amma tana kallon yadda rayuwar d'iyarta take d'ai d'aicewa....bansan ma ya akayi rayuwarki ta tsaya a haka ba!....bansan waye ya tsaya miki ba!….” ta fada da qaraji kaman zata yage maqogoronta. "Allah" Amsar da zaiso bata kenan.....amma ya zabi yaci gaba da tsaiwa behind the curtains and doors indai batayi yunqurin taba mata lafiya ba. Akhnan ta ja baya da sauri kamar an mareta numfashinta ya rikice,kalaman sun mata nauyi da yawa. “me kike cewa?....kinsan me kike cewa?." Mammina kai tsaye da kallon nan tsirararsa ta zuba mata idanu . "Ke ba 'yata bace!.....har abada!" "Ke alama ce kawai ta tozarcin safeena a gareni!" Akhnan ta soma girgiza kai cikin kuka. Gaba daya tana jin an dawo da quruciyarta yanzu tana rushewa daya bayan daya. Kowacce runguma?,kowacce nuna qauna?,kowacce kulawa?,kowanne murmushi?,kowacce soyayya fake ce?!.....jabu ce?!.....ba gaskiya bace?!. “kinyimin qarya.....” “ta shekaru da dama...…” "Qwarai.....kuma na tsallake ba" Ta fada da iszgili a muryarta. Sai ta juya baya a hankali "Soyayya ba ita ke tafi da masarauta ba........power ce!" Ta fada tana watsa mata wani kallo. "Kina zaton soyayyar malamin can zata kubutar dake.....kina tsammanin d'an gidan ibraheem zai zame miki garkuwa?" Ta tambaya wata dariya na bayyana saman fuskarta. "Kina ganin kin tsallake duk shirina a kanki?,.....ba zaki tsira ba Akhnan.....baki da gata a yanzu....baki da wanda ya tsaya miki.....sai yadda naga daman juya akalar rayuwarki". Hannayensa ya dunqule,yana qoqarin hana kansa afkawa chamber din,da qyar ya dawo da control dinsa. Akhnan tayi wata irin tsaiwa a wurin kamar wadda aka cirewa numfashi,wani irin ringing Kunnuwanta sukeyi kamar masu shirin kurumcewa. Zuciyarta na bugawa kamar wadda ke shirin kamuwa da ciwon zuciya. “Kin san me yafi bani dariya?” ta tambayeta ba tare da ta juyo ba “Yadda kika dinga kallona da idon soyayya shekaru.” kalaman suka fita da sautin qaramar dariya a muryar mammina din. *_wai wai wai.😭😂.....lallai.....mara kunya yaji dadinsa. Ya Allah ka rabamu da makantar zuci.....kasa mufi qarfin zukatanmu_* *_muje zuwa dai....saimun warware zaren duka in sha Allah_*😭😭 *zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 08187255862 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 08187255862 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 118* __________________________ ✨ AMINTACCEN GURIN SIYAN THRIFT ABAYAS ✨ Ingantattun Thrift Abayas masu kyau da tsari akan farashi mai sauƙi da araha. Muna kawo sababbin kaya akai-akai tare da rangwame na musamman. 🤍 Dukka sai a MK ABAYA BOUTIQUE 🤍 Duniyar Thrift Abayas masu kyau, masu tsari, da salo iri-iri domin kowane lokaci da kowane irin event. Abayas masu inganci, masu salo, masu araha, kuma na zamani ga mata masu son ƙawata kamanninsu cikin kamala da kamun kai. Karki bari a ba ki labari... Leƙo ki ga yadda MK ABAYA BOUTIQUE kullum ke cike da kyawawan Thrift Abayas akan farashi mai kama da kyauta. 'YAN SARI, 'YAN REPOSTING, DA MASU SIYA DON AMFANIN KANSU... DUKA INA MUKU MARABA! 🤝🤍 📱 WhatsApp: 07064399623 📞 Call: 08036027448 🔗 Join our Wholesalers Group: https://chat.whatsapp.com/JBg80RmA47v7GoqvWdgLJT?s=cl&p=a&mlu=3 ___________________________ Girgiza kai akhnan tayi,wasu irin zafafan hawaye suna wanke mata fuska “Don Allah kiyi shiru…” ta fada cikin karyewa. Ji take kaman zatayi hauka.....kaman kwanyarta tana damulewa a duk kalma daya da zata fito daga bakin mammina. "Abinda yake sake bani dariya shine......yadda kika dinga gudu zuwa jikina a duk sanda wani ya b'ata miki rai ko ya miki ba daidai ba....." Cak kalaman mammina suka tsaya cikin iska.....komai na quruciyarta yana dawo mata ana mata kamar wadda aka kunnawa faifan rayuwarta. Daga kai tayi ta sake kallonta.....tamkar ba itace wannan matar data tab'a rainonta ba?. Tamkar ba itace wannan matar data kira UWA ba. "Ashe baki taba sona ba?" Ta fada tana zubawa mamminan idanu,tsantsar karaya suna nunawa cikin idanun nan nata da ruwan hawaye yake kwarara. Murmushi tayi,irin murmushinnan me sanyi wanda yafi mari ciwo "Na gaya miki ai....amma inajin kina buqatar maimaici ne.....so ko?.....kinsan me ake kira soyayya a fada?" "Rauni" Ta qarasa maganarta. "Amma kina rungumeni....kina cemin d'iyata" Akhnan ta furta cikin fitar hayyaci tare da jin komai yana zame mata kamar mafarki ko wasan kwaikwayo. Juyowa tayi tana kallonta sosai,Idanunta babu taushi ko kad'an “Ko kina tunanin rungumar da nake miki na gaskiya ne?” sai ta saki wata dariya me ciwo “Duk lokacin da na kalleki…” “…ina ganin fuskar uwarki." Riqe qirjinta akhnan tayi,numfashinta na sarqewa. "Ki tsaya.....don Allah ki tsaya" Ta fada tana fatan ta tsaya din,tana fatan kuma ya zama mafarkinne. Saidai ko alaman ta tsaya ba tare data amayar ta tsiyayar da dukka magangun bakinta batayi ba. "Uwarki ta samu abinda nakeso......wato sultane...." "Tsahon shekarunnan yana bauta mata saboda sanyi da taushin halinta.....tsahon kuma shekarun da suka biyo bayan mutuwarta din ya gagara mantawa da ita duk da tarin kyautatawata a gareta,safiyya taxo ta sake lullube wannan gurbin da nake harin samu....." "Na tsani yadda yake kallonta....." Ta fada muryarta na cracking. "Na tsani yadda ya kasa mantata" Ta sake fada wannan zallar wutar qiyayyar na nunawa qarara cikin idanunta. Sake takowa tayi gabanta. "Da Gaske na girmar dake.....saidai ki tuna,kowanne halin kirki nawa qwara d'aya.....yaqine ga mataccen jikin safeena". Wani irin baya akhnan taja,tana jin yadda quruciyarta ke rugurgujewa a gabanta. Mammina ta gyara mata gashi sau ba adadi.....ta rungumeta sanda tana kuka.....ta tsaya mata a gurare masu tarin yawa.....mafi girma ta kirata da D'IYATA.....duka wannan FAKE NE?!.....qarya ce?. "Ya zama dole a kanki ki godemin.....don na barki da ranki ba kaman yadda na salwantar da wasu ba.....na barki kin rayu cikin daular mulkin mahaifinki......ba kaman yadda na hana 'yan uwanki zama cikin tasu daular ba.....ahmad d'an sultane da safeena......da kuma d'an AJANI jinjirin da bashi da suna" Sai ta fara takawa da wani irin taku dake nuna zallar rashin imani a tare da ita "Ke wace irin macace?" Akhnan ta fada a tsawace tana jin yadda take sake tarwatsewa a gaban mammina. Murmushi ta sake mata tana duban fuskarta. "Mace me son nasara......abinda ya hanani cinyeku tunda wuri.....shine sultane.....yanzu kuma babu shi.....ba wanda ya isa ya dakatar dani daga dukkan shiri na....." "Daga yau.....kada ki sake kallona a matsayi uwa!" Ta fada tana takawa zuwa qofar da zata fiddata a gurin. "Saboda nima ban taba kallonki a matsayin d'iya ba......sannan....." Sai ta dakata. ".....ki shirya.....kece plan dina na qarshe.....ba kuma wanda ya isa ya kareki" Tana kaiwa nan ta bude qofar ta shige tana maidata ta kulle. Yana jin takunta......yana jin takun wucewarta......amma baima kalleta ba,saboda dukka hankalinsa yana kan kowanne fitar numfashin akhnan da komawarsa. Qirjinsa na masa wani irin ciwo,yana jin kamar bazai dauka ba.....kaman iya abinda zai iya dauka kenan. Akhnan red line dinsa......wanda tabbas idan mammina ta sake ta qetarashi,komai zai sake muni sama da munin da yake dashi a yanzu. Kasa motsi akhnan tayi,kamar jikinta ya manta yadda ake numfashi. Kamar qafafuwanta sun daina daukar nauyi. “Mijina ya kasance nata kafin na zama komai…” “Murmushin da nake miki yaqi ne…” “Na rainaki ne saboda kina tuna min ita…” Kalaman suna ta maimaituwa cikin kanta. Idanunta suka soma rawa. Kwanyarta ta kasa karbar abinda taji,sai numfashinta ya fara qoqarin rikicewa. "Aah.....aah....aah" Haka ta fada a jajjere tana dora hannunta akan bakinta wai ko zata iya hana kanta zubda hawaye. Gaba daya qirjinta taji yana mata ciwo,kamar an tsaga an ciro wata tsoka daga muhallinta. Sai ta juya da sauri ta fito daga chamber d'in. Cikin takunta na tangal-tangal,kamar wadda tasha wani abun maye ta bugu. Hawayenta kawai sauka suke ba qaqqautawa. Cikin tsoro hadiman suke matsawa suna sauke idanunsu qasa daga kallon matar sheikh muhammad haisam din. A yanayinta kawai basu tab'a ganin rauni a tattare da ita ba irin na yau. Ta kai qarshen corridor din da qyar,sai qafafuwanta suka kasa daukarta. Ta dafe bango da qarfi. Numfashinta na rawa. A lokacin ne yake sake takowa zuwa gareta,cikin sassarfa da karsashi da tarin kuzarin nan nasa wanda a yau yakejin kamar ya zarta kullum,kamar jinin da zuciyarsa ke bugawa zuwa ga gangar jikinsa na yau ba irin na ko yaushe bane. Qamshin nan nasa shi ya gaya mata shine ya iso gabanta. Ta d'ago idanunta tana dubanshi......suna hada idanu sai wani sabon kuka mai ciwo ya kubce mata. “Haisam…” ta fada da wannan sautin da yakeso,saidai a yau wannan muryar ba irin wadda yake da muradin ji bace. Bata iya jira ya risketa a inda take tsaye ba,ta soma takawa zuwa gare shi da sauri. Kamar mutum mai neman mafaka. Kafin ta isa din qafafuwanta suka sake tangal-tangal da ita. Tareta haisam yayi da sauri. Ya mata kyakkyawan riqo kafin ta kai ga fad'uwa. Da qarfi ta kama rigarsa ta riqe sosai cikin hannunta,yanayi riqon daya zame masa ma'auni na girman zafi da rad'ad'in da takeji a zuciyarta. "Tayimin qarya......tasa na qare girmana tana yaudarata". Kallon fuskarta haisam yayi.....kumburarrun idanunta....rikicewar numfashinta kawai sai suke neman d'auke tasa nutsuwar. Ya sake matse haqoransa yana qara tilastawa kansa controlling abinda yakeji din. "Me tace miki?" Ya tambaya cikin sanyin murya kaman baiji komai ba. Jikinsa ta shige sosai......dukka jikinta yana rawa. Daya bayan daya ta gaya masa.....sak yadda mammina ta fada baiji ta mañta ko ta rage abu ko qwara daya ba. “Ashe duk shekarun nan…” ta fada ko ina a jikinta yana rawa. “…ni ba d'iya bace a wajenta…” . Hannunsa ya dago,ya riqe bayan kanta a tausashe. Ya jawota jikinsa sosai kamar yana qoqarin tattara dukkan b'angarorin zuciyarta da suka tarwatse. “Ki kalle ni.” ya furta da wata sirrintacciyar murya me taushi. Sai ta d'ago idanunta cikin hawaye kamar yadda ya buqata. “Abinda mugun mutum ya kasa bayarwa…” ya furta yana share mata hawaye “…ba yana nufin baki cancanci shi bane.” wasu sabbin hawayen ne suka sake bin kuncinta bayan wadanda ya share mata. Kamar wuta haka yake jin d'igarsu har cikin tsakiyar zuciyarsa. "Kinjini?" Ya fada yana tattaro fuskarta a tsakiyar tafukan hannayensa. "Rashin soyayyarta......" Ya fada da muryar rad'a. "Ba laifinki bane" Sake riqe hannayensa tayi sosai tana girgiza kai hawayen sun kasa controlling kansu suma. "Na yarda da ita.....na qaunaceta" Wani kallo me taushi ya bayyana a idanunsa. "And that says more about your heart…” "Than hers........" Ya qarasa fadi yana jin yadda numfashinta ke a rikice kamar zuciyarta ta kasa d'aukar nauyin gaskiyar da taji. Da wani irin taushi ya mata muhalli me kyau a qirjinsa,ya kuma lullubeta da dogayen hannayensa,ya mata rumfa ruf ta yadda ta bace gaba daya a faffadan qirjinsa. Yana jinta,tana son sakeyin magana,sai ya lumshe idanunsa yana furta. "Shshshsh..... Ki bari numfashinki ya daidaita tukunna" (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) Qara mannewa tayi cikin jikinsa,tana sauke wani irin kuka me nauyin gaske. Hannunsa saman kanta yana shafawa a hankali har zuwa gadon bayanta. Idanunsa suna runtse,yana jin yadda bugun zuciyarsa ke sake motsawa da wani irin nauyin gaske. "Bansan me yasa yakemin zafi ba......ya kamata na tsaneta yanzu" Ta fada muryarta na sarqewa da kukan. "Ki tsaneta......ki tsaneta gwargwadon yadda zaki iya.......is allowed" Ya furta da wani taushi a muryarsa,idanunsa har yanzu a kulle. Ya fahimci ciwon da take ciki,mutum mafi kusa da ita tun tana yarinya...... ashe duk shekaru yana rayuwa da qarya......me yafi wannan ciwo?. "Zakiji ciwo giiftii.....zakiji ciwo sosai....." "......Mutum mai zuciya mai tsabta idan aka cuce shi…” "...…ciwon yakan zurfafa.” Ta girgiza kai tana kuka a hankali. “Na kira ta uwa…” Sai ya share hawayen gefen fuskarta da babban yatsansa yana dubanta a nutse. “Kuma kin yi hakan da zuciya d'aya ba.” ya sake karkatar da kansa yana kallonta cikin idanunta “Kar ki ji kunyar hakan.” sai ta sauke idanunta qasa. “Amma ni wawiya ce…” tayi maganan muryarta tana rawa. Yatsunsa ya sanya,ya dago habarta a nutse yana jin kalmar data gayawa kanta da kanta ta masa ciwo. “Kada ki sake fad'ar haka.” yadan kausasa muryarsa. “Kin ji ni?” Ta kalleshi cikin rawar ido irin na wanda ke qoqarin dakatar da hawaye. “Mai yaudara ne yake da laifi.” ya fada yana cusa tafin hannunsa cikin nata. “Ba wanda ya bada gaskiyarsa ba.” hawaye ya sake gangaro mata ta dukkanin idanunta biyun. Sai ya jawota jikinsa yana matseta sosai da wani irin dumi da taushi daya mamaye ilahirin jikinta. Ya bari ta yi kukanta. Bai hanata ba. Saboda ya san: 👉 wasu ciwukan hawaye kad'ains suke iya rage su. Na wasu seconds corridor d'in ya yi shiru. Sai sautin kukanta kad'ai,da bugun zuciyar Haisam da yake ji har kunnuwansa. Ya bata tazara da ratar mintuna kafin ya motsa a hankali,ya d'an sunkuya kusa da kunnenta. “Mu tafi?.” ya tambaya kamar me mata rad'a. Sai taji zuciyarta ta harba tana skipping na wasu sakanni daga aikinta. “Ba zan barki a nan ba.” ya bata tabbaci yana sake gyara mata hijabinta daya sake fdda wannan marainiyar fuskartata. Sai ya riqe hannunta cikin nasa. Ba kamar yadda yake yi kullum ba. A yau.....riqon nasa ya sake zama na musamman. Tamkar yana gayawa duniya da ita dashi kansa cewa. NINE GARKUWARTA NA HAR ABADA. Ita dinma Ta kasa sakin hannunsa ko da sau d'aya. Kamar idan ta sake shi,zata sake fad'uwa ne....faduwar da ba ranar sake tashinta. Da kansa haisam ya bud'e kofar. Ya jima da tsaida da kima dakatar da wata hidima duka data shafi akhnan din. Komai......kusan komai dasu birra ke mata shi yakeyi yanzun. Yayi tasa yayi nata. Takanji nauyinsa idan ta ganshi kitchen......yana dafa mata tea ko madara. Batasan wanne baiwa Allaj ya mata ba.....wacce irin nau'in kyauta Allah ya mata daya bata irin wannan LU'U LU'U da yafi komai tsada cikin nau'in kadara. Billionaire irin wannan......ita diyar muhammad hammud tayi sanadin shigarsa kitchen yana mata hidima?. Mutumin da idan yaso inda kuma yana da ra'ayi.....cook kowanne iri ne zai iya hiring ya kawoshi kawai don ya masa girki. Yana lura da hakan,akwai kuma sanda ya rutsata da narkakkun idanun nan nasa,ya sanyata a tsakiya yana tareta da hannunsa ta hanyar dafe cabinet din kitchen din da hannuwansa. "Kin dauka da wasa ne......idan nace miki ina karantaki ta idanunki?" Kai take qoqarin kawarwa saboda yadda kwarjinin nan nasa ke bugunta. "A duniya babu wanda yakai muhammadurrasulillah daraja......duk duniya sun shaida haka ne?" Ya fada yana d'age girarsa. Kai ta gyada a hankali. "Amna yana tsayawa a gidansa,ya taya matansa hidima". Maganan ta sauka a kunnenta da wani irin ma'ana da cikakken nutsuwa. Daga ranar.....daga lokacin wani girmansa ya sake ninkuwa a ranta da idanunta. Ko a labari.....ta jima bataga mutum me matsayi irin nasa ba,amma kuma bai dauki kansa a bakin komai ba. Ya shigar da ita ciki yana kaffa kaffa da ita. Dakin yayi duhu mai laushi,nutsuwa.......da wata irin kwanciyar rai a cikinsa. Ya sake matsawa ciki,sai ya cire alkyabbarsa ya aje gefe. Ya juya gareta. Har yanzu tana tsaye kusa da qofa kamar bata san me zatayi ba. Kyawawan farare kuma blue eyes dinnan jajur da alamun kuka. *zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 08187255862 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 08187255862 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 119* ________________________ ✨ AMINTACCEN GURIN SIYAN THRIFT ABAYAS ✨ Ingantattun Thrift Abayas masu kyau da tsari akan farashi mai sauƙi da araha. Muna kawo sababbin kaya akai-akai tare da rangwame na musamman. 🤍 Dukka sai a MK ABAYA BOUTIQUE 🤍 Duniyar Thrift Abayas masu kyau, masu tsari, da salo iri-iri domin kowane lokaci da kowane irin event. Abayas masu inganci, masu salo, masu araha, kuma na zamani ga mata masu son ƙawata kamanninsu cikin kamala da kamun kai. Karki bari a ba ki labari... Leƙo ki ga yadda MK ABAYA BOUTIQUE kullum ke cike da kyawawan Thrift Abayas akan farashi mai kama da kyauta. 'YAN SARI, 'YAN REPOSTING, DA MASU SIYA DON AMFANIN KANSU... DUKA INA MUKU MARABA! 🤝🤍 📱 WhatsApp: 07064399623 📞 Call: 08036027448 🔗 Join our Wholesalers Group: https://chat.whatsapp.com/JBg80RmA47v7GoqvWdgLJT?s=cl&p=a&mlu=3 __________________________ A hankali ya qaraso kusa da ita. Ya dago hannunsa ya sake gyara mata hijab din daya dan zame cikin kulawa. “Kin ci wani abu yau?” Ta girgiza kai. “Bani jin zan iya…” “Zaki iya.” ya amsata calmly “Ko kad'an ne.” sai ta sauke idanunta. “Bana jin cin komai yanzu…” Sai ya d'an yi shiru yana kallonta da wani irin taushi mai nauyi a idanunsa “Then borrow my strength tonight.” Ta d'ago idanunta gare shi a hankali. “Har sai naki ya dawo." Ya furta yana lumshe idanunsa gami da budesu a cikin nata. Wannan kalaman nasa,suka sake karyata. Yana da wasu irin kalamai....a idanunsa da harshensa wasu irin dafi ne da ba wanda zai gane sai wadda ta jarabtu dashi......sai wanda yake tare dashi. Tarin hikimar zance me laushi da nutsuwa.....wanda ke iya sanyaka ko ya hanaka abinda duk kayi niyyar yi. Sai ya ja ta zuwa sofa gently ya zaunar da ita. Ruwa ya miqe ya dauko da kansa,ya dawo ya tsugunna gabanta yana zuba ruwan da kansa. Ta bishi da kallo......yana sake shiga zuciyarta da wani irin qarfi da shi kansa bai sani ba. "Madalla da miji na gari" Ta fada tana sake jin kamar zuciyarta zata karye sanda ta tuna sultane shine tsanin samun wannan lu'u lu'un me tsada a gareta. Wanda ya yarda yayi kuka tare da ita.....suyi dariya tare. Wanda ya yarda ya tsaya a gefanta ba tare daya durqushe ko ya tsuguna ba. "Take it" Ya fada yana miqa mata tambulan na glass cike da ruwan idanunsa masu sanyin nan cikin nata. Ya jira har ta sha kad'an. Ya karba ya ajiye,sai taga ya jawo plate din abinci da bata lura da sanda ya zubashi ba. Kai ta langabe sai shima ya mata yadda ya saba,yadda yakewa nanay dinsa,dole ta sauke nata makamin duk da ranta baya so. Cikin nutsuwa har ta ci spoon uku. Cikin bata kulawa kamar yana kula da abu mai rauni da zai iya karyewa. Shi ya tsaya tayi wanka.....shi ya tsaya ta sauya kaya,ta zauna gefen gadon cikin shiru......shurun da ya dauketa ya cillata wata duniyar tunani da mamakin da har yanzu bai saketa ba. . Kamar zuciyarta ta gaji da kuka haka takeji. A nutse haisam ya zauna kusa da ita,sanye da lausasan pyjamas da kyansu ya sake fitowa saboda daddadan qamshin nan nasa dake kadawa. Qamshin kuwa yayi nasarar isa zuwa ga hancinta kai tsaye,ya kuma aike mata da wannan nutsuwar da ya saba aje mata a dukka sassan jikinta. Na d'an lokaci babu wanda yayi magana,sai shuru daya wanzu tsakaninsu,suka barwa zukatansu saqe saqensu. Sai ya d'ago hannu ya kamo nata da wani irin taushi da nutsuwa. Ya miqa dogayen yatsunnan nasa yana shafa bayan tafin hannunta a hankali. Numfashinta taki yayi nauyi......taji ya soma saukar mata da wata irin tsumammiyar kasala a dukka gangar jikinta. Tadan saci kallonsa,idanunsa suka d'an gutsira mata wani abu daban. "Kinga d'a namiji.....bashi da haquri a fagen mu'amalar aure......musammanidan yana samun dukkan yadda yakeso....kuma idan har ya d'an d'ana yaju yadda abun yake......bazanji kunyarki ba.....zan fada miki.....mijinki da dukkan yaqini zai iya kasancewa a wannan sahun" Ta tuna wata magana da nanay ta taba gaya mata,wadda sai da taji inama ace qasa ta tsage ta shige?. “Ki kwanta.” muryarsa ta sauka a kunnenta softly. Idanunta ta bude a hankali,ba wannan maganan ta dauka zataji daga bakinsa ba,akwa abubuwa masu nauyi danqare data hanga cikin idanun nasa......amma me yasa ya zabi gaya mata iya wannan?,koda ba zata magance masa da komai ba. kai ta girgiza kai kad'an,tana jin tausayinsa yana saukar mata a hankali. Yayi kawaici.....ya kauda kai akan komai......bayan tasan can qasan ransa yana da buqatuwa zuwa gareta.....wacce irin sadaukarwa ce wannan?. “Idan na rufe idona…” muryarta tayi rauni,tana jin zata fada masa ne don shi kadai ya rage mata a duniya. “…zan sake jin muryarta.” Wani irin abu ya motsa a zuciyar Haisam me ciwo,sai ya matsa kusa da ita kad'an. Ya d'ago hannunsa ya shafi gefen kanta. “To kada ki yi yaqi da tunanin.” ya fadi calmly “Kiyi tunaninki gwargwadon yadda zai ishi kwanyarki ta bari ya wuce.” sai ya dakata yana kallon fuskarta da kullum kwanan duniya sai yaga abinda ya burgeshi.....sai yaga abinda ya masa kyau. “And every time it hurts…” ya saka hannu yana share wani sabon hawaye “…look at me.” Sai ya ja ta jikinsa a hankali. Da wani irin rauni ta kwantar da kanta a kafad'arsa shi kuma yana riqe da ita cikin nutsuwa. Mutsuka tafin hannunta yaci gaba dayi,ta daidai gurin da yake da connection da idanuwa da sanya bacci. Batasan me yakeyi ba,tasan dai tana jin dadin wadannan tafukan hannayen cikin nata. Sannu a hankali kasala ta fara saukar mata,idanunta suka fara nauyi. (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) "Kwanta" Ya fada yana gyara mata pillow. Ba musu ta kwanta,yaja mata comforter yana lullubeta sosai. Idanunta a lumshe sanda yake shafeta da addu'a. Taja numfashi sosai,tana jin yadda hannuwansa suka yita son sauya akala da tsaiwa a wasu gurare da yawa a jikinta,abinda ya haifar mata da kasala kenan,ya kuma so tayar mata da nata tsumin daya tsuma mata a ranarsu ta qarshe a dubai. Ta dauka zai fita ne yayi uzurinsa bayan ya gama mata addu'ar.....amma maimakon haka sai taga ya jawo abin sallarsa bakin gadon ya zauna akai kamar wanda aka bawa gadinta. Bai matsa mata da magana ko yawan kallo ba.....ya bata space sosai yana raba hankalinsa tsakaninta da littafin hannunsa. A haka ya zauna da ita tsawon dare. Yana shafa kanta lokaci zuwa lokaci. Yana duba yanayin baccinta. Yana gyara mata gashi idan ya rufe mata fuska. Yana lallashinta idan hawaye suka sake kufce mata. Kamar duk aikinsa na daren nan guda d'aya ne....... Tabbatar da cewa Akhnan bata ji ita kad'ai bace a duniya ba! *_Nima a nan nace MADALLAH DA MIJI NA GARI IRIN HAISAM_* ★★★Tun bayan kalaman mammina zuciyar Akhnan ta kasa samun sukuni. Duk sanda ta rufe idonta,sai ta ji muryarta tana dawo mata kamar a sannan take fada. “Ban tab'a kallonki a matsayin d'iya ba…” Amma abin da ya fi kashe mata zuciya ba wannan kadai bane. A’a. Yanzu ta fara tuna yadda aka rabata da morsa safiyya tun tana yarinya. Yadda aka sanya aka kuma maidata me tsananin yi mata rashin kunya. Yadda aka cusa mata qarya shekaru masu yawan gaske,ta kuma girma cikin wannan qaryar. D'aya bayan daya abubuwan da suka faru a shekarun suka fara dawowa mata. Tana qin zuwa sashenta. Tana jin haushinta ba tare da dalili ba. Yadda mammina ke nuna mata Safiyya a matsayin barazana a fakaice cikin hikima da dabara bawai kai tsaye ba. Yanzu kuma.... wadda aka hanata ta qaunata… ita ce ke prison saboda qarya makirci da tuggu?. Wannan tunanin ya soma cin Akhnan daga ciki. Ta kasa cin abinci yadda ya kamata. Ta kasa bacci. Takai koda haisam yana kusa da ita......zuciyarta na ci gaba da nauyi. A safiyar ranar,daya tsareta da wadannan narkakkun idanuwan saman dining table,inda suke zaune daga shi sai ita. Ya zuba mata komai yana cin nasa a hankali yana monitoring dinta da d'aurarriyar fuska. Tun kalaman farko da yace. "Kina cutar dani da rashin cin abincin nan......kinaso mu rusa rayuwarmu ne gaba daya?". Bai sake cewa komai ba,saidai da wannan qwarewar tasa yake tilasta mata cin abincin ta hanyar sarrafata da idanunsa. Batajin taste din komai,kaman yadda komai baya mata dadi. Morsa safiyya kawai take burin gani,wanda a yau tana jin ba zata tsallake yau din bata ganta ba. "Zanje wajen momma" Ta fada muryarta a qasa. Haisam dake gyara cufflinks d'insa bayan ya gama shanye nasa tea din ya dago idanunsa gareta. Ya lura da yadda muryarta take rawa. "Akhnan" Ya kira sunanta na asali,maimakon giiftii....my princess....my healer da yafi kiranta a yanzu. “A’a.” ta fada da sauri tana girgiza kai,saboda ji tayi kaman yana shirin cewa ba zataje bane. “Ba zan iya zama a nan ba.” “She’s alone because of me.” ajiyar zuciya me nauyi haisam ya saki,sai yaja kujerarsa sosai yana d'an matsawa kusa da ita. “Ba saboda ke bane.” ya fada yana bata assurance da idanunsa. “Da ban yarda da Mammina ba tun farko…” hawaye na taruwa mata “Da ban dinga cutar da momma ba…” Sai ta dafe kanta ta taji yana sara mata. “Ya Allah......Allah…” Ta fada sautin yana komawa can cikinta. “Yaya zan kalleta yanzu…” a hankali haisam ya kama hannunta a tausashe,ya kuma game da nasa tafin hannun yana bata therapy dinnan dake nutsar mata da d'imautar zuciya. “She knows who poisoned your mind." Yayi maganan da faransanci,kalamansa a jejjere kaman wanda ya shiryasu kafin ya fadesu. “She never blamed you.” Sai ta girgiza kai,tana jin kamar ba haka ba. “nice abar zargi.....ni kaina ina zargin kaina da kaina.” shuru yayi,baisan ta yadda zai cire mata wannan ba kuma,baisan ta yadda zai gamsar da ita ta daina zargin kanta ba,ya kuma tabbatar inde ba morsa safiyya ce ta fada da bakinta ba ba zata aminta da hakan ba. "Ka barni naje.....i.need to see her" Hannunsa dayan ya sake azawa saman nasu yana damqewa sosai. "And if this is exactly what Mammina wants?.....ta fada,kece next target nata.....ko ba haka tace ba?" "Ban damu ba......ban damu ba haisam a yanzu......abinda na sani kawai morsa safiyya......she's alone" Sai muryarta ta karye. "…and I left her alone for years.” ta qarasa fada hawaye yana gangaro mata. *zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 08187255862 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 08187255862 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 120* _________________________ https://chat.whatsapp.com/BkfPzSEDhnsIwyCD8LNGkm?s=cl&p=a&mlu=0 *IDAN KINSAN BA ORDER DIN KAYA ZAKI DINGA SAKAWA BA* *IDAN KINSAN BA BUSINESS KIKE DA NIYYAN YI NA KAWO KAYA DAGA CHINA BA KARKI SHIGA* *_DON ALLAH KARKI BATAWA KANKI LOKACI_* *_Assalamu alaikum my loyal people_* *_Barkanmu da wannan lokaci,kuma barkanmu da warhaka_* *_akwai da dama cikin mata wadanda suke sha'awar yin order kaya daga CHINA zuwa NIGERIA,NIJER,CAMERON,CHAD da GHANA_* *_Amma rashin samun amintaccen company....ko hannun wanda zasu dinga siyan kaya ta hannunsu cikin aminci ya hanasu_* *_To a yau addu'ar da yawa daga cikinku ta amsu,don nayo muku tsarabar kamfanin da zakuyi siyayya ta hannunsu su kuma dora muku kayanku har qasarku cikin aminci ba tare da fargaba ko d'ar d'ar ba_* *_kunsan komai nawa TASTED AND TRUSTED ne,to wannan kamfanin idan akwai abinda yafi TASTED AND TRUSTED ma shine_* *_Baki da fargaba kota sisin kwabo,ni SAFIYYA HUGUMA na tabbatar da hakan_* *_Zaki iya kasancewa dasu group nasu,inda a nan zaki hadu da agent dinsu da CEO nasu gaba daya ta wannan link din,zaki samu bayanansu da komai da ya shafi mu'amala dasu_* *INA ME BAKU TABBACIN AMINCI DA INGANCI DA SAUQIN MU'AMALA DASU DA IZININ ALLAH,BAN TALLATA MUKU SU BA SAI DANA GWADA* *Allah ya dafa mana,yasa mana albarka a nemanmu,ya albarkaci halal dinmu ameen summa amee* _________________________ Wani irin zafi na fitar hawayenta ya ratsa haisam.....Saboda ya san,wannan guilt d'in ne zai fi kashe ta akan komai. Yatsansa ya santa yana dauke mata hawayen. " You're not your childhood mistakes......you were manipulated" "Amma ai i still hurt her" Ta fada sabbin hawaye suna zuba a fuskarta. "And now she’s in prison while I’m here…” Jawota yayi jikinsa ya rungumeta a nutse,yana shafa bayanta a hankali gami da maimaita fadin. "Hasbunallahu wani'imal wakeel" A hankali ta kama da bakinta tana maimaitawa Sallamar birra da wata irin murya me cakude da tsoro yaja hankalinsu. Sai data shigo sannan suka lura,ba muryarta kadai ke rawa ba.....dukka ilahirin jikinta ne yake rawar. "Jami'an tsaro ne......sunce gurin gimbiya sukazo" Ta fada jikinta yana rawa gaba daya. Tunda take a agadez bata taba ganin masifar data sanyata jin kamar ta gudu ba irin wannan lokacin. "Kije kice zamu fito yanzu" Haisam ya fada calmly,da wannan nutsuwar tasa dai data zame masa tambari,tamkar babu wani abu da aka gaya masa me daga hankali. Juyawa yayi ga akhnan,sai yaga ta zuba masa idanu. Tashin hankali ne kwance cikin idanunta tana dubansa,amma ga mamakinta sai ya sauke mata tattausan murmushin nan nasa. "Me kike tsoro?,koma meye karkiji tsoro muddin haisam yana tare dake.....no one is taking you anywhere idanma abinda sukazoyi kenan.....not while I'm standing". Hannunsa ya miqa a nutse,ya dauki hijab din daya cire mata dazun da hannunsa ya ajiye gefansa sanda zasuci abincin,yana dan tsokanarta sanda ya zare mata hijabin "Komai ma an tattare an hanamin......wannan beautiful gorgeous face and body dinma hiding mani shi ake?" Murmushi ya bata a sannan,wani sassanyan murmushi mara kuzari ko kadan. A yanzunma.....da kansa ya dagata,ya kuma saka mata shi ya daure mata igiyar,sannan ya riqe hannunta softly suna takowa a hankali zuwa bakin qofa. Dab da bakin qofar suka tsaya,ya soma karanta addu'ar fita a gida ba tare daya kalleta ko yace komai da ita ba. A hankali ta kama itama har suka kammala tare,suka sanya qafafuwansu zuwa waje a tare kuma lokaci daya da bismillah. Taka qwallewar tana tsakiyar qwayar idanunsu haka fitowar tasa ta kasance musu dukkaninsu gaba dayansu. Su bashi suka buqaci gani ba.....akhnan ce. A nutse yake binsu da kallo,jami'ai ne saidai kuma shima nashu guards din sun zagayesu cikin shirin kota kwana. Wannan yaqin ba nasu bane,baya kuma fatan sanya kowa a cikinsu,don haka da idanu kawai ya musu umarni suka janye suna bacewa daga gurin. D'aya daga cikin jami'an ya matso,don tafiyar wadancan mutanen sai sukejin ya zame musu wata babbar dama da zasu aiwatar da aikin yadda akeso. "Gimbiya akhnan......an buqaci ki biyomu". Maganar tasa ta tsaya cikin iska tana yawo. Akhnan ta tsaya cak tana dubansu,jikinta yayi wani irin sanyi. Ta fahimta.....sai yanzu ta sake fahimta.......ita ma ta shiga jerin wad'anda Mammina take son rushewa. Sai ta ji yatsun Haisam sun qara matse nata a hankali. Gargadi ne......wani kakkausan gargadi da zaiso ace sun fahimta tunda wuri......tun lokaci bai qure musu ba. Haisam bai kalli jami’in nan take ba. Idanunsa na kan Akhnan. Yana kallon yadda numfashinta ya rikice. Yadda tsoro ya soma shiga idanunta. Sai ya d'an matsa gabanta kad'an bayan ya saki hannunta. Nan take ya koma GARKUWA.....nan take ya shimfida katanga tsakanin ganinta dasu. Wadannan idanun......idanun nan dake cike da wani shimfidadden kwarjini ya daga a kansu,take dukkaninsu sukasha jinin jikinsu......kowanne kuma yanayin da yakeji a jikinsa da zuciyarsa ya sauya. Ya musu kwarjini.....me yawan gaske. Basusan waye ba.....baqin haya ne,shigarsu gidan na farko kenan akan aiki na musamman da ogansu yace zasuyi cikin agadez. Ta zabi dauko bare na waje.....saboda tasan duk cikin agadez babu wanda zai iya tunkarar wannan aikin haka kai tsaye ba tare da tsoro ko shakka ba. Bausan waye ba.....amma kallon Haisam yanzu ba irin wanda suka saba gani bane. “Wa ya aiko ku?” ya fada da wata irin nutsuwa dake gauraye da fushi. Saida jami'in ya hadiyi yawu sannan yace. "Giwa ce.....giwa mammina ce ta bada umarni......" "Naji!" Haisam ya yankeshi ba tare daya barshi ya ajiye bayanin ba,duk da ba dabi'arsa bace hakan. Wani irin shuru ya ratsa gurin. Sai Haisam ya d'an karkatar da kansa. Nasa salon aikin dake cikin jini ya motsa,ya soma karantar yanayinsu shigarsu dama nutsuwarsu,irin qwaqwafin nan na masu binciken qwaqwaf da suka saba. Idanunsa suka sauka kan takardar dake hannun jami’in. “Da wace hujja?” ya tambayeshi yana zare idanunsa daga kan takardar. Jami’in ya soma rikicewa kad'an,don har cikin hanjinsa yakejin kallon “Ana zarginta da.... ” “Na ce ba!…” haisam ya datseshi da kakkaifar muryar nan tasa. “Da wace hujja?” ya sake maimaitawa yana zube musu idanunsa yana binsu da kallo daya bayan daya. Guards d'in suka soma kallon juna. Saboda ba su tab'a jin mutum irin Haisam ba. yana magana haka kamar ba kamu sukazo yi ba akan laifin da ake tuhumarsu dashi. Takardar hannunsa jami'in ha miqa yana rawar murya,yana jin kamar bazai iya ci gaba da tsaiwa a gurin ba. “Royal order ne…” Haisam bai karb'a ba ma. Sai ya kalli seal d'in kawai sannan yayi murmushi kad'an. Wani irin murmushi mai razanar da zuciya. “She’s getting bold.” ya fad'a muryarsa can qasa. A hankali Akhnan ta d'ago idanunta tana saukesu a kansa.Ta fara jin wani abu daban a yanayinsa. DANGER!!!.....shigen wanda ta gani a sanda TAMIM yayi nufin keta iyakarta. Barin inda yake tsaye yayi,yayi taku biyu gaba.....takun daya sanya guards d'in saurin jaa baya,tamkar sun hangi zaki ya tunkarosu. Da wani irin kallo yake binsu,yana jin naman zuciyarsa yana motsi. “Ku koma ku gaya mata wani abu." Yayi maganan calmly kamar ba shine zuciyarsa ke zabalbala ba. Ba wanda ya iya koda motsa yatsarsa,sai ya sake magana. A hankali. Amma kowace kalma nada wani irin kaifi dake iya fede zuciya saala saala. “Ahmad…” ya irga da nutsuwa sosai. “Safiyya…” “…na ƙyale ta.” Akhnan ta tsaya cak,saboda yadda muryarsa ta canza. “Na ƙyale ta tana wasa da iko…” ya fada yana tsuke idanunsa sosai launinsu yana sake jirkita zuwa yanayin da suke komawa idan yana cikin tsananin fushi da b'acin rai. “Saboda tana tona kanta da hannunta.” gaba daya suka qarasa daskarewa a gurin da jin irin saqon da yake aikewa mammina. Sai ya d'an juya kadan. Ya kamo hannun Akhnan gaba d'aya cikin nasa. Riqon hannun da su kansu saida suka bi hannuwan nasu da kallo.....wani abu cikin kansu da zukatansu yana gaya musu SAQO NE DAGA ZUCIYAR WANI ZAKIN MAZA. “But this woman?” Ya furta yana dubansu,duba irin na kai tsayen nan wanda babu sassauci a cikinsa. (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) “MATATA CE!!!.” Wani irin shiru me ban tsoro ya sake ratsawa. “And if Mammina has forgotten…” ya fada da wani nutsuwa me karya qashi da zuciya. “…ku tuna mata.” Sai ya matsa gaba kad'an. “Akhnan…”ya kira sunan Lower voice,amma cike da wnai respect cikin kiran sunan kawai. “…ita ce layin da babu wanda yake tsallakawa!!!.” Kamr jininsu ya tsaga ya ajiye wannan saqon haka sukaji. Jami’in da yake shine shugaba sai yarasa yadda zai hd'iye yawunsa. Har a jijiyoyin jikinsa yakejin wannan ba gargadi bane kawai.......RANTSUWA CE!!!......ALQAWARI NE. Hannunsa ya sanya,ya karb'i takardar daga hannun jami'in finally. Ya kalla na second biyu. Sannan ya zame yatsunsa daga na akhnan,ya yayyagata gida biyu. Akhnan ta zaro ido. Gaba daya Guards d'in kowa ya shiga wani irin shock. Saboda babu wanda ya tab'a karya umarnin Mammina haka a bude a bayyana a gaban jama'a. Saki takardun yayi suka zube k'asa iska tana sake d'ai d'aitasu a gurin da wani yanayi na rashin daraja da tozarci. “Ku fita.” ya fada calmly. A karon farko babu wanda ya motsa saboda tsoro. Sai ya d'an d'aga gira kad'an. “Ko sai na manta cewa ku kuna aiki ne kawai?” Sunkuyar da kai sukayi da sauri,suka kuma soma retreating da sauri. Amma saidai kafin jami’in ya fita,haisam ya sake kiransa. “Tsaya.” Mutumin ya tsaya a take kamar yadda ya buqata,sai haisam ya zuba masa ido da wani irin sanyi mai kashe jiki a idanunsa. “ka fada mata wannan da kyau.” ya furta a hankali “Na yi shiru saboda na yarda.” “Kar ta tab'a kuskuren tunanin na kasa tsayarda ita.” dukka gurin ya dauki shuru “Saboda ranar da zata sa ni shiga tsakaninta da Akhnan…” ya damqe haqoransa har hakan yana nuna alama ta saman kumatunsa,ya kuma dunqule hannunsa yana son boye azalzalar da zuciyarsa ke masa. “…ita ce ranar da zata fahimci ban tab'a shiga yaqi da ita ba tun farko.” taku uku yayi ya basu baya ba tare da sake umartarsu su fita ko su zauna ba. Kamar masu turereniya suka soma fita,kamar suna son barin wajen kafin wani abu ya faru. Tsaiwa kawai akhnan din tayi tana kallonsa. Tsahon saninta dashi.....tsahon sanda ta fara ganin fuskarsa idan ka cire randa tamim yaso tafka wannan gangancin bata taba ganin fuskarsa a haka ba. Wani irin sautin bugu zuciyarta take bayarwa. "Ya salaaammm......ya ilaheeee" Ta fada cikin zuciyarta. Zaki ta nema.......sai kuma ta samu sama da abinda yafi zakin. Jarumta.....qarfin zuciya da zallar kwarjini me yagalgala zuciya. A hankali ya juya gareta,nan take yanayin idanunsa ya canza,ya sake komawa wannan haisam din......SOFT HAISAM da take gani kowacce rana.....ba wanda ya gama magana yanzu haka a gabanta ba. Sai ya d'ago hannu ya shafi gefen fuskarta cikin kulawa. “No one will touch you.” ya fada da dukkan zarrarsa. “Na miki alqawari.” ya sake tabbatar mata. A yinin ranar gaba daya,wani yanayi daban take gani tattare da haisam din. Wani abu ya sauya a cikinsa...... Ba a fuska ba. Ba a kalamansa ba.Amma a idanunsa… akwai wani irin yanke hukunci da ya fara bayyana. Kamar zuciyarsa ta gaji da jiran lokaci. A daren ranar.......akhnan ta soma lura da kowanne canzawar motsi na haisam. Kad'anne.....wata irin kakkaifar alaqar zuci data qullu tsakaninsu ba tare da dukkaninsu sun ankara ba ya sanya take gane komai nashi a yanzun. Yawanci idan dare yayi yakan kasance kusa da ita. Ko yana karanta wani abu. Ko yana karatu a library dinsa. Ko kuma kawai yana zaune yana kallonta idan ta kasa bacci. *zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 08187255862 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 08187255862 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 121* ___________________________ *_Amintaccen gurin siyayya_* *_ingantattun kaya akan ingantaccen farashin da ba irinsa a kasuwa_* *_BONONZA DA PROMO akai akai_* *dukka sai a HUGUMA CLOSET* *Duniyar kayan yara,mata,maza,dukka* *shaddodi,atamfofi,laces,abayas,jakankuna,takalma,agogo,sarqoqi,English wears,night wears,under wears,da duk wani nau'in sutura babba da qarami* *_Karki yadda ayi babu ke.....leqa kiga yadda closet din HUGUMA kullum ke cike da kaya akan farashi me kama da KYAUTA_* *_YAN SARI....YAN REPOSTING.....DA SARAKAN ADO MASU SIYA DON KANSU....DUKKA INA MUKU MARABA_*🤝🤝🤝🤝 https://chat.whatsapp.com/FrqgC0YmUWP4FPmUzYuLJX __________________________ Amma a yau yawan fitarsa ya qaru. Wayarsa tayi ringing da yawa sama da yadda ya saba ji. Yana amsa wayarsa cikin low voice. Yana fita balcony. Ko ya shiga private study. Dogayen calls,muryarsa low da wani irin controlled a cikinta. Ko kusa.....ko alama bata d'auka zata tsaya koda a gefan wannan matsayin da take ganin ya azata ba. Bata taba zata ko tunanin matsayinta yakai har yau haura haka ba sai a yau din. Saboda ita.....saboda ita kawai ya rasa dukka nutsuwarsa?. Cikin dare sau biyu tana farkawa ba tare da ta ganshi kusa da ita ba kaman yadda ya saba. Ta miqe a hankali tana sauka daga gadon,ta shiga toilet tayi fitsari. Shi yasa takejin wani emptiness a cikin baccin nata,ashe rashinsa ne a kusa da ita?. Mamaki ya sanyata sakin murmushi duk da jagulewar da har yanzu zuciyarta take ciki game da lamarin mammina. Tana fitowa daga toilet din sai ta hango haske a kunne ta corridor. Ta taka a hankali ta tsaya bakin qofar. Idanu ta zuba sosai,qofar bata kammala rufuwa ba,akwai siririn space da yayi ragowa,wanda ta nan ne hasken ya samu daman fitowa. Ta nan din ta hangeshi,idanunta ya sauka a kansa a hankali. Haisam zaune cikin dim light. Files da takardu sun cika table din dake gabansa. Wayarsa a kunnensa. Wani old map a buɗe gabansa. Qasa qasa takejin muryarsa,wannan muryar da yau tun dazu amonta ya canza da wani launi na daban. “No.” ya fada da low and cold voice “I said before sunset” sai yayi shuru yana sauraron dayan b'angaren. Ya motsa a hankali yana daga wata takarda yana kallonta. “Everything must be ready.” “No mistakes.” Idanunta ta lumshe tana kuma budesu lokaci daya dukka a kansa. Duk wannan yaqin da akeyi hakan bai hana soyayyarsa ginuwa cikin ranta ba. A yau yadda yayi matan sai ta sake jin tafi kowacce mace sa'ar samun miji da ba irinsa. Sai ta jita tana komawa sarauniyar matan duka duniya....bawai sarauniyar agadez kawai ba. Bata tab'a ganinsa cikin irin wannan tension din ba. Komai na iya taku da tsaro yabi jikinsa.....don haka a jikin nasa yaji kamar motsinta. Baya taja kadan,sai kuma taga qofar ta bude. Haisam ya fito. Sanye da black qatar thobe da bai rufe maballan gabanta ba,wannan ya sanya lallausar gargasar dake qirjinsa a kwance ta fito. Hannunsa ya sanya a hankali yana shafa gurin maballan,shima ya manta.....ya mañta a bude suke tun dazu,sau yasa hannunsa daya da yatsunsa yana qoqarin ballewa. Kunya ta kamata,ta dauke idanunta gefe. Hala yaga tana kalle masa qirji shi yasa ya ankara da bai balle ba yake ballewar. Idanunsa suka sake sauka a kanta instantly. Na second biyu,tsigar jikinsa na tashi a hankali saboda yadda farar night gown din ta mata kyau ta kuma karbeta duk da kaurinta,gashin gaban goshinta ya fito sosai ya kwanta,ya sake fidda kyanta. “Me yasa baki kwanta ba?” yayi tambayar calmly. Akhnan ta kalleshi cikin shakku. “Kai fa?” ta fada softly “Tun ɗazu baka huta ba.” Sai ya d'an yi shiru. Kallon da yake mata yanzu,cike yake da tunani “Akwai abubuwan da ya kamata su motsa kafin lokaci ya kure.” ya fada da tattausan sautin nan nasa. “Wane irin abubuwa?” ta tambaya cikin rashin fahimta tana matse girarta. Ta masa kyau....wani irin mugun kyau,sai ya kasa riqe kansa ya matsa kusa da ita a hankali. Hannu ya daga yana gyara mata gashinta daya biyo ta cikin dankwalinta me santsi ya kwanta gefan kunnenta,sannan ya sake gyara mata zaman dankwalin. Gentle habit nasa data lura dashi kenan,yana killace komanta. “Things that should’ve been done earlier.” idanunsa take kalla,wadannan idanun masu taushi da tsananin haske,amma a yanzun idanun sunyi nauyi,kamar bai yi bacci ba kwata kwata,cakude da wani boyayyen sirri. “Haisammm…” ta kirashi da sound da yanayin nan da yakeso a muryarta. “Me ke faruwa?” Sai ya zuba mata ido na wasu seconds. Wani irin kallo mai zurfi. Kamar yana jin ciwon ganin ta cikin wannan halin yake sake kallonta sosai. “Trust me a little longer.” bata gane ba....sam bata fahimci me yake nufi ba,wannan amsar tasa,ta qara mata rud'ani. Ta sani......haisam baya roqon trust,yawanci kawai yake daukar mataki ne. Sai ta zabi ta matso kusa da shi. “Yana da alaqa da Mammina?” ta tambaya kai tsaye. Ya matse haqoransa guri guda. “It has to do with ending this." Sai ya kamo hannunta ya sanya cikin nasa. Yanason wannan kyakkyawan lallausan tafin hannun. “Ki koma ki kwanta" Ya fada yana murza mata bayan hannunta a hankali. “And no matter what happens tomorrow…” “…stay beside me.” saita tsaya kallonsa,tsalle zuciyarta takeyi. Me kuma zai faru goben yake neman hakan a tare da ita?. Zata rasashi ne?,shin zata rasashi ne kaman yadda ta rasa komai da kowa nata?. Idan ta rasa kowa ta iya jurewa.....anyaaaa......anyaa zata iya jumurin rasashi?. "And no matter what happens tomorrow… stay beside me.” ta sake maimaita kalmar,saboda yadda ya fadi maganar. Kamar mutum mai shirin shiga wani yaqi ne. “…Tomorrow?” ta tambayeshi a fili. Haisam bai amsa nan take ba,sai ya sauke idanunsa kan hannunta dake cikin nasa,kamar yana tunanin abubuwa masu yawa a lokaci guda. “Some truths…” shuru “…change everything.” qara rikitata yayi. “Haisam…” ta sake kiransa tana sake hade tazarar tsakaninsu. Tsoro takeji.....bataso komai sabo ya sake tasowa a yanzu. Cikin matsala masarautar take sosai.....basa buqatar qarin wata. “Kana bani tsoro.” Sai ya dago idanunsa zuwa cikin nata a hankali da wani lallausan kallo. “I’m trying to protect you from it.” Sai ta kalleshi cikin shiru,saboda yadda yake magana yau daban yake da sauran ranaku da lokuta. Kamar yana bankwana da wani zamani ne. (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) Iskar dare na motsa labulen corridor din a tausashe. Wani irin shuru ya rufe tsakaninsu. Idanunta dake narkewa a kansa suka lura da gajiyarsa. Fararen idanun nan da suka zama jajaye. Yadda kafad'unsa suka sake. A hankali ta d'aga hannunta ta taba gefen fuskarsa. Karo na farko cikin kwanakin nan,taji ita takeson lallashinsa ba yadda shi ya saba yi mata ba......ita ce take son ta kwantar da damuwarsa. “Ka huta kad'an…” cikin murya me kama da rad'a,duk da rudanin da tunaninta ya shiga. “Please.” ta qara da fadin hakan ganin yana tsaye kawai yana kallonta. Ya lumshe idanunsa na second daya da hannunta a fuskarsa. Kamar tabashin kad'ai yana rage masa wani abu. Ya bud'e idanunsa a hankali,sai ya kamo hannunta ya sumbaci bayan tafin hannun nata a tausashe. “After tomorrow.” cikin low voice “I’ll rest after tomorrow.” ya fada cikin coolness. Wannan kalmar tasa,ta sake bugun zuciyarta da qarfi. Saboda ta fara jin wani tsoro da fargaba sosai akan kalamansa. Ta matso jikinsa da wani irin sanyi,ba tare data furta kowacce kalma ba,ta jingina kanta a qirjinsa,wani yanayi dake bata nutsuwa. A nutse da taushin nan nasa haisam ya sauke hannunsa a bayanta,da wani yanayi na bada kariya ta gaske. Na wasu seconds babu wanda yayi magana. Bugun zuciyarsa ke sauka a kunnuwanta,da wani yanayi me sassauci a cikinsa. Abinda ya fi bata nutsuwa a yanzu. “Ka yi min alqawari." muryarta can qasa “Ba zaka barni cikin duhu haka ba.” Sai ya sauke habarsa a saman kanta. “I promise…” da dakusashiyar murya irin ta me rad'a “…when it’s over, you’ll know everything.” "Komai?” ta tambaya da zaquwa a muryarta. Juyo da ita yayi sosai suna fuskantar juna,sai idanunsa suka tsaya cikin nata. Da zuzzurfan kallon nan.....da wannan gaskiyar da take gani ko yaushe fal idanunsa. “Komai" Ya bata tabbaci. A hankali ya riqe hannunta yana tafiya da ita zuwa room bedroom din. Wannan lokacin,ba kamar wanda yake lallashin mai kuka ba,aah....da wani irin tattalinta suke takawa. Ta zauna gefen gado tana binsa da ido yayin da yake cire agogonsa. Yana aje wayarsa. Yana sake duba wani saqo da ya shigo. Kuma duk lokacin da screen din wayar ta haska,fuskarsa qara yin serious take. Ta runtse idanunta na taqaitaccen lokaci. FARGABA....fargaba takeji sosai,cikin sanyin murya tace. “Haisamm…” “Hm?” ya amsa,amma bai juyo ba tukuna “…duk ko me kake shiryawa…” sai ta dakata kafin ta qarasa da sanyin muryar dake cakud'e da tsoro. “Ka dawo min lafiya.” ta qarasa fada muryarta tana rawa,zuciyarta na motsi a cikin qirjinta. Haisam ya tsaya cak. Kalmarta ta sauka a zuciyarsa da nauyi. A hankali da tarin nutsuwar nan tasa ya juya gareta. Kallon da yayi mata yanzu,ya fi kowanne taushi. Sai ya qaraso kusa da ita. Ya sunkuya gabanta. Ya d'ora goshinsa a nata. “There is nowhere in this world…” “…I would go without coming back to you.” ya fada suna musayar numfashi shi da ita. *_Uhmmmm😍🥰🥰,ita wannan soyayyar......koda a filin yaqi suke inajin ba abinda zai dakusheta_* *_to dani daku sai nace mu jira goben.....muga abinda goben zatazo mana kuma dashi_* *zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 08187255862 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 08187255862 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 122* _________________________ *_Amintaccen gurin siyayya_* *_ingantattun kaya akan ingantaccen farashin da ba irinsa a kasuwa_* *_BONONZA DA PROMO akai akai_* *dukka sai a HUGUMA CLOSET* *Duniyar kayan yara,mata,maza,dukka* *shaddodi,atamfofi,laces,abayas,jakankuna,takalma,agogo,sarqoqi,English wears,night wears,under wears,da duk wani nau'in sutura babba da qarami* *_Karki yadda ayi babu ke.....leqa kiga yadda closet din HUGUMA kullum ke cike da kaya akan farashi me kama da KYAUTA_* *_YAN SARI....YAN REPOSTING.....DA SARAKAN ADO MASU SIYA DON KANSU....DUKKA INA MUKU MARABA_*🤝🤝🤝🤝 https://chat.whatsapp.com/FrqgC0YmUWP4FPmUzYuLJX ___________________________ *SECRETS BENEATH THE CROWN*👑 Tun a asubahin ranar masarautar agadez dama wajenta ya cika da sanarwa me matuqar qarfi data girgiza hankali da tunanin kowa. GIWAR AGADEZ mammina.....na gayyatar duk wani isashe wanda ya isa ya fada aji cikin agadez dama masarautar zuwa kotun masarautar domin yanke hukunci. Hukunci akan AKHNAN......d'iya ga sarki sultane. Hukuncin da ba na komai bane......face ta raina umarnin masarauta........ta wulaqanta dokar masarauta ita da mijinta......ta kuma yaga takardun aike na fada wanda babban laifi ne aikata hakan. Ba'a aikesu musu direct ba......saidai ya tsinci maganan sanda yake fita zuwa sallar asuba. Sallar asuba da shine ya jagoranceta a asubahin wannan ranar. Idanunsa cike da bacci.....gangar jikinsa fal gajiya,kansa yana sara masa da masa ciwo kadan kadan,to amma a duk sanda zuciyarsa ta tuna masa gagarumin abinda zai faru a safiyar ranar sai yaji gajiyar da baccin dukka sunyi nasu guri. Ya shigo ya samu akhnan saman abun sallah. Yanayinta ya canza ba kaman sanda ya fita ba. Ya zargi taji wani abu.....amma kuma inda taji din yana kyautata zaton tashin hankalinta da rud'aninta zaifi yadda yake gani a yanzu tattare da ita. "Ta hada taro don zartarmin da hukunci" Ta fada tana duban fuskar haisam daya zauna a hankali saman sofa. Idanu yadan zuba mata,kafin a hankali ya miqa hannunsa ya riqe nata a ciki. "Wannan jarumtar da nake gani a yanzu cikin idanunki.....daga ina?" Yayi maganan da wani salo daya sanya murmushi qwace mata. Tadan murmusa kadan,duk wutar dake ruruwa a zuciyarta me tsananin gaske,amma zuwa yanzu.....tana jin yarda dashi,tana jin aminci a dukka kalaman daya gaya mata daren jiya. Bayan wannan kuma......a yanzun tana jin ta shirya fuskantar komai......ta shirya fuskantar kowacce rayuwa da zata zo mata. Ta sauke fararen blue eyes dinsa a nutse a kansa. "Tunda ina auren jarumi......dole ne nima na zama jaruma ko?" Maganan ya sanya wani tattausan murmushi subuce masa. Ya zuba mata idanu sosai idanunsa suna lumshewa gami da bude kansu da kansu. "Na gode.....na gode da wannan amincin.....da wannan shaidar" Ya fada yana gyada kai. "Ba abinda zai sauya alqawarinmu na jiya......zaki zamana a gefe na kaman yadda zan zama a gefanki......komai dadi komai wuya.....har abada" Kai ta gyada masa a hankali,sai ya sakar mata hannu a hankali,ya sake miqa hannunsa ya dauki wani alqur'anin ya miqa mata. Bata musa ba,ta saka hannuwanta dukka biyun ta karba,ta bude daidai iya yadda karatunta yakai,ta fara karantawa kamar yadda taji yana rera karatun a nutse da wannan lallausar muryar tasa da zata iya sanya mutum manta damuwar da yake ciki. ★ Babban courtyard na masarautar Agadez cike yake da jama'a. Dattawa. Masu fada aji. Guards. Talakawan dake rayuwa cikin masarauta,kuma qarqashin kulawar masarautar. Kowa ya hallara. Wani irin farinciki takeji.....wata irin annashuwa da walwala,musamman idan ta aza idanunta akan duk mutanen dake zaune a gurin,taga kowa yana zaune ne bisa umarninta.....yana so ko baya so. Kowa biyayya yakewa umarninta yana so ko baya so. Kowa gudun saba mata yakeyi da dadi ko ba dadi. Taja iska sosai tana jin cewa.....yau zata kauda katanga ta qarshe......yau zata zubda katanga ta qarshe da zata qarasa bata cikakkiyar dama qarasa tattarewa da nade tabarmar data shimfida na rayuwa cikin agadez na shekara da shekaru. Saidai idan ta juya inda tasa aka shirya don akhnan da mijinta su tsaya su fuskanci hukunci,taga gurin empty. Ta kalli agogo taga yadda suka shanya ta. Ba ita kadai bama kowa da kowa sai taji ranta ga baci. Dole ne ta tozartashi shida matarsa a yau din,a bainar jama'a. Dole ta bashi guzurin da zai isa Ethiopia dashi.....guzuri mafi muni kafin ta tattara ta bishi a qarasa yaqin a can. Safiyar ranar da mammina zata fito ta yankewa Akhnan hukunci a gaban fada. Private royal chamber dinsu ya yi shiru. Daga waje ana jin motsin guards. Surutan bayi. Motsin mutanen da suka cika courtyard din. Saidai tana magana kowa yaja bakinsa ya tsuke yana saurarenta. "A shaidawa akhnan cewa......ba zamanta muke a nan ba.......ta gaggauta fitowa zuwa gaban hukunci" Juyawa me isar da saqon yayi yana fita da gaggawa. Daga can sassan haisam.....cikin qawataccen bedroom din nasa dake da wani yanayi na nutsuwa. Kaman a jininsa ne.....komai nasa nutsuwa yake nunawa. Koda doki ne.....muddin mallakinsa ne zaka ganshi da wannan tambarin. Akhnan ce tsaye gaban babban mirror din d'akin,sanye da wani elegant dark royal attire. Black da deep gold. Wani luxury hijab ta dora a sama na luxury silk mai laushin da yake nuna matsayinta.......matsayin nan na sarauniyar agadez......matsayin nan na akhnan muhammad hammud.....suna da matsayin da ba wanda ya isa ya qwaceshi. Haisam ne......haisan da kansa ya zabar mata wadannan kayan......wannan shigar......tamkar yanason amfani da wannan damar ya tabbatarwa da duniya matsayinta. Tayi wani irin kyau.......amma duk kyawun da tayin idanunta sun gaji. Irin gajiyar dake bayyana kanta koda anyi nufin boyeta. A yau tana ji a ranta zata rasa komai. Tana ji a ranta yau mammina zata gama da ita kaman yadda taso. Hannunta na rawa kad'an yayin da take qoqarin gyara bracelet d'inta. Wannan bracelet din na azurfa wanda ke maqale da adon lu'u lu'u a jiki.......wannan bracelet din me girman matsayi da daraja wanda aka bata daga Ethiopia randa ta saka qafafunta cikin masarautar. Saidai amma ta kasa rufewa. A hankali hannayensa masu taushi suka karba gently,yana tsaye daga bayanta,irin tsaiwar data bada wani irin kusanci na sosai a tsakaninsu. Ba tare da magana ba,ba kuma yare da yace komai ba,ya d'auki bracelet d'in. Ya rufe mata shi a hankali. Kamar wanda yake handling glass. Ita dashi dukkaninsu suka fito tarwai ta mirror din,ya nuna su tare. Shi cikin all black royal attire. Perfectly tailored dake nuna zallar sanin darja da mutuncin ado da iya sanya sutura. Agogon silver dinsa ya zauna sosai saman lallausar fatarsa. Azurfa qwaya daya data sanshi da ita tsakiyar hannunsa dake da adon wani dutse na lu'u lu'u dakesheqi yana sauya colors. Aura d'in nan tasa mai had'a......power.....danger da calmness. Ta d'ago idanunta ta kalleshi ta cikin madubin,tun safe zuciyarta a matse take. Ahmad yana prison......morsa safiyya tana tsare.....a yau kuma.......yau ita mammina keson hukuntawa cikin bainar jama'a. Ta sake nutsar da idanunta a kansa. Ba wani alamun tsoro fargaba ko d'ar saman fuskarsa. Sai wata irin sassanyan nutsuwa a tare dashi. Har yana da karsashi da kuzarin tsokanarta a dazun. “…Ya kamata mu tafi.” ta hada kalaman a nutse labbanta suna motsawa da wani yanayi daya masa kyau sosai. Idanunsa ya zare a hankali daga kanta,sai ya ci gaba gyara cuff ɗin hannunsa calmly,kamar baya cikin gaggawa ko kad'an “Not yet.” Ta haɗe gira kadan tana motsa fuskarta. Wannan halin nasa.....wannan dabi'ar ta sanya komai da kowa su jirasu....kaman a wannan gurin bata dace ba. “Haisam…” ta kirashi da wannan sound din nata. (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) “Everyone is waiting.” Sai ya d'ago idanunsa sosai yana sanyasu cikin nata. “Let them wait.” ya amsa da wata nutsuwa. Wani irin bugun zuciya ta ji,saboda yadda yake calm yau. Too calm. "me yasa ba zamu tafi ba?" Ta tambaya. Tanason suje akan lokaci ne,saboda kada mammina ta tsammaci tsoro ko rashin gaskiya tattare dasu. Kyawawan idanunsa ya lumshe sannan ya budesu a kanta gaba daya.....kyawawan fararen idanun nan da a yau taga kamar sun qara haske. "Because timing matters". Ta matsa kusa da shi sosai. “You’re scaring me again......tsoro kake ban.....tsoro nake ji har cikin jikina". Shuru kawai yayi,sai ya zuba mata ido na wasu seconds. Kamar yana kallon wani abu mai daraja sosai sosai.....kamar yana qiyasce tsadarta da darajarta ga rayuwarsa. A hankali ya d'aga hannu ya gyara gefen hijab dinta da ya dan zame. Wannan dabi'ar tasa dai,kaffa kaffa da komai nata. “Look at me.” Ta daga idanunta gare shi,sai ya riqe hab'arta a tausashe. “What do you see?” sai ta dan rikice,idanunsa suna mata kaifi da yawa. “…You.” Wani lallausan murmushi ya tab'a lips d'insa a taqaice. “No.” sai ya sake takowa shima yana hade tazarar dake tsakaninsu. “tsoro kike ji.” “And I need you to stop.” sai ta runtse idanunta kad'an......saboda gaskiya ne. Tana jin tsoro,da gaske ne. Da gaske ne,ya karanta cikin zuciyarta ta idanunta kamar yadda ya saba. “rusheni takeson yi.” ta furta muryarta tana rawa. “She already destroyed everyone around me…” Sai Haisam ya girgiza kansa a hankali. “Listen to me carefully.” sai yayi qasa da muryarsa kamar wani sirri ne a tsakanin shi da ita. “No one destroys you while I breath" Zuciyarta ta buga da qarfi,saboda yadda ya fadi kalaman dab da kunnuwanta. Ya kamo fuskarta dab da tashi sosai har numfashinsu na had'uwa "Kin tsira daga abubuwa da yawa.....abubuwa masu yawan gaske.....abubywan da suka fi wannan muni da girma....." “You survived betrayal.” “You survived grief.” “And today" Ya furta tana kulle idanunsa cikin nata. “…you survive the truth.” Idanunta ta lumshe a nutse,tana jin yadda kalamansa suma samu gurbi me kyau cikin zuciyarta......tana jin yadda kalamansa suke bata qwarin gwiwa. “What does that mean?” Sai ya yi shiru......a hankali ya d'ora goshinsa a nata. “It means…” cikin muryar rad'a “…by tonight, nobody will ever make you bow your head in this palace again." Hawaye suka cika idanunta,saboda yadda yake magana kamar ya riga yaga gobenta. Yadda yake bata tabbacin tsaro da aminci. Sai ta kamo gaban rigarsa a tausashe,zuciyarta da muryarta suna rawa. “What if I break today?. Idanunsa ne sukayi wani irin duhu,kamar kalmar ta taba wani sashe me girma ma zuciyarsa “Then break in my hands." Ya furta da Fuskarta cikin tasa,hancinsu yana gogar na juna,yana riqe da qugunta sosai cikin hannuwansa. “Not alone.” ya qarasa fadi muryarsa na fita da wani irin nauyi. Wani irin numfashi ta sauke,tana jin ruhinta.....jarumtarta da dukka nasararta ta ta'allaqa dashi. Sake riqeta yayi sosai cikin jikinsa,da sautin nan na rad'a dake ruguza kowacce garkuwa ta jikinta. “And when we walk into that courtyard…” ya fadi a nutse. “I don’t want fear in your eyes.” Sai ya d'an sunkuya kadan zuwa saitin tiny lips dinta. “I want them to see the wife of Haisam.” ya qarasa fadi da wani yanayi da taji kamar qafafunta ba zasu iya daukarta ba. Wani irin d'umi ya ratsa zuciyarta. Sai ya miqa mata hannunsa. “Ready?” Ta kalli hannun nasa. Then ta daga idanunta gare shi. Still tana jin wani tsoro.....saidai jarumtar daya bata ta mamaye wannan tsoron da wani irin qarfin gaske. A hankali ta sa hannunta cikin nasa. “…Ready.” Sai Haisam ya dan matse hannunta. Kuma a karon farko yau,wani abu kamar relief ya bayyana a idanunsa. *zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 08187255862 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 08187255862 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 123 A* __________________________ *_Amintaccen gurin siyayya_* *_ingantattun kaya akan ingantaccen farashin da ba irinsa a kasuwa_* *_BONONZA DA PROMO akai akai_* *dukka sai a HUGUMA CLOSET* *Duniyar kayan yara,mata,maza,dukka* *shaddodi,atamfofi,laces,abayas,jakankuna,takalma,agogo,sarqoqi,English wears,night wears,under wears,da duk wani nau'in sutura babba da qarami* *_Karki yadda ayi babu ke.....leqa kiga yadda closet din HUGUMA kullum ke cike da kaya akan farashi me kama da KYAUTA_* *_YAN SARI....YAN REPOSTING.....DA SARAKAN ADO MASU SIYA DON KANSU....DUKKA INA MUKU MARABA_*🤝🤝🤝🤝 https://chat.whatsapp.com/FrqgC0YmUWP4FPmUzYuLJX ___________________________ Cikin qasa da minti daya kaf guards nasa da security dinsa suka zagaye kotun,da wani irin salo da qwarewar aiki,wanda ba lallai kai da kake gurin ma ka fahimci su waye zagaye daku ba. Bada uniform ba ballanta ka ganesu,saidai kwanya da horaswar da suka samu daga yarima muhammad haisam kadai abar kallo ce. Sun riga da sun tabbatar da tsaron gurin,kuma suna cikin shirin kota kwana......su dakatar kosu afkawa duk wanda yayi yunqurin yin wani abu na ba daidai ba.....ko duk wanda yake shirin cutar da yarimansu ko matarsa akhnan. Wani irin kiran hankalin mutane sukayi sanda suke takawa cikin chamber din. Kamar wadanda aka gayyata walimar girmamawa.....ba wadanda aka gayyata don hukunci ko tuhuma ba. Bada kalma sukaja hankalin kowa ba ko daya.....bada wani sauti ba.....aah....zallar kwarjinin sheikh muhammad haisam dake haskawa da wani irin qyalli cikin idanun duk wanda ke iya ganinsa. Sanda yake takowa hannunsa a bayyane cikin na matarsa.....gimbiya akhnan muhammad hammud...... Riqon daya mata....kamar yana gayawa kowa cewa. A shirya yake yayi komai saboda ita,....a shirye yake ya bada fansar rai da rayuwarsa.....a shirye yake kuma yayi fito na fito da duk wanda ya qalubalanceta. Mammina dake zaune daga garinta ta gani.....taga komai.....ta kuma fahimci komai. Ta dinga qoqarin saisaita kanta,don daga kallo daya tak daya mata yaso birkita tsarinta da tunaninta na yau. "Wannan idanuwan ibraheem ne" Ta fadawa kanta tana qoqarin controlling kanta. Bai tsaya gaban kowa ba....bai magana da kowa ba har sai daya isa mazaunin da aka tanada masa shi da akhnan. Ya riga ya tabbatar da tsaronsa. Don haka kai tsaye ya dorata saman kujerar cikin girmamawa,shi kuma ya koma bayanta ya tsaya kamar wani badakkare daya shirya bada rayuwarsa saboda qasarsa da al'ummarsa. Wata irin tsaiwa dake nuna mutuntawa da bada cikakkiyar kariya.....wata tsaiwa data tsayewa mammina cikin idanu da zuciya. Mammina din ce ta miq tsaye cikin,cikin shigar nan tata da kowacce daqiqa take nuna izzar mulkin da ake tattalinta kowacce rana. Ta d'aga kanta da isa. A yau,tana jin kamar finally ta mallaki komai ta kuma mallaki kowa. "Wannan masarauta tana zargin khadeeja muhammad hammud da karya dokokin masarauta masu tarin yawa....ko a yanzun da taqi amsa kiran masarauta a sanda ta kirata alama ce ta raini da tozarci.....kafin sannan......ana zarginta da laifukan hada kai masu cin amanar rawani da masarauta gaba daya......" Sai ta dakata tana duban fuskar akhnan don son tantance meye akai. TSORO take buri da muradi gani......amma ga tarin mamakinta shine.....irin shigen nutsuwar da take ganinta akan fuskar safiyya......irin tarin nutsuwar da take gani game da haisam,itace a yanzu take gani akan fuskar akhnan din. Ba digon tsoro ko gigita sam akan fuskarta. Ta sauke idanunta tana ci gaba da karantawa,tare da bawa kanta tabbaci. Ba yadda za'ayi taji hukuncinta na gaba ba tare da sun gigita ba su duka. “Bisa ga dokokin masarauta…” murya na fita cikin courtyard din. “…duk wanda ya had'a kansa da masu cin amanar masarauta...." “…ba shi da gurbi a gidan nan.” Akhnan ta runtse idanunta,zuciyarta na bugawa da wani irin ciwo. Ita ake nufi za'a barranta?......ita ake nufi za'a kora daga da'ira da ikon mahaifinta?. Mahaifarta....inda cibiyarta ke a binne?. Muhallin da duk duniya bata da kamanshi?. Ba'a tsada ko alatu ba.....aah.....GIDA wani abune na daban da ba kowanne muhalli ke iya maye gurbinsa ba. Hannun haisam ta matse a hankali,sai shima ya matse nata cikin nasa da wani irin taushi,saidai bai motsa ba,bai kuma barta ta motsa ba kwata kwata,idanunsa kafe kan mammina. "Ba yanzu ba.....yi haquri.....sauran 'yan mintuna" Ya fada yana matsa device din kunnensa muryarsa can qasa. Da yake baya ta bashi,ta dauka da ita yake,saita sake aro nutsuwa ta azawa kanta tana sauraren komai da bugawar zuciya. “Daga yau…” ta fada tana nuna akhnan kai tsaye da yatsarta. “…an cire ta daga duk wani iko da alaqa da masarautar Agadez!.” Hayaniya......wata irin hayaniya ce ta tashi. Falaak ta fashe da kuka......falaak din dake zaune cikin ciwon data rasa musabbabinsa. Tana jin kamar duniya takewa bankwana.....tana jin kamar kwanakinta sun qare a duniya. Wani hukunci ne da yazo musu da girma da nauyi. Qananun qus qus har a sashen dattawa ta fara tashi. Saidai kuma.....kowa tsoro ne fal idanu da zuciyarsa. Kowa baya da iko na cewa komai.....kowa baya da iko na daga harshensa ko hasashensa akan maganan. Hannu mammina ta daga.....abinda ya sanya duk wani cecekuce dakatawa,shuru kama anyi ruwa an dauke. “Kuma idan ta qi bin umarni…” ta fada da izza tozarci da gadara. “…za’a kaita prison kamar sauran ‘yan tawayesu." Nan take guards suka soma matsowa kusa da inda akhnan ke zaune. D'an motsawa kawai haisam yayi ya saka guards tsayawa da wani yanayi na shakka da tsoro a fuskarsu. Mammina ta lura da hakan,Idanunta suka hadu da nasa. “Ko kai ma zaka tsaya gaban dokar masarauta?” ta masa tambayar tana jin a daidai wannan lokacin tafi sha'awar maganarsa akan shurunsa. Wannan shurun.....wannan shurun dake razanata da hanata bacci a dukka darare. Ta tuna shi alsaamit ne.....alsaamit kuwa da shurun aka sanshi.....saidai shurunsa kuma hadari ne. Tasha qiyasta da wanne hadari shurunsa zaizo muta?. Duk da tana jin ta shirya......ta shirya ta kowacce fuska ta wanne bangare da yake tunanin zai iya zuwa mata. Shuru gaba daya gurin yayi.......tamkar kowa na jiran amsar Haisam. Ya d'aga idanunsa a hankali zuwa fuskarta. Bataga digon FUSHI BA a ciki....wani abu daban ta gani. Wani abu da yafi fushi tasiri.....wani abu da yafi fushi razanarwa. “Dokar masarauta?” ya tambaya irin tambayar nan ta kai tsaye......irin tambayar nan ta titsiye. “Ko son ranki?” wata hayaniya ce ta sake tashi. Wani tasiri ta ji a cikin jininta.....tasirin QASQANCI da wannan kalmar da haisam din ya jefeta da ita. Ba wanda ya taba dubanta ya gaya mata wata kalma da bata amintar da ranta ba da muradinta saishi......shine mutum na farko.....kuma tunda har yayi wannan gangancin.....to tabbas zata tabbatar daya zama mutum na qarshe.....zatabar tarihi a kansa.....tarihin daba wanda zaiyi marmarin kwatantawa. “Ka manta wa kake magana da shi?." “A’a.” ya amsa mata kai tsaye kuma a taqaice. “Ke ce kika manta iyakarki.” ya amsa mata yana duban tsakiyar idanunta. Dukkanin tarin qasqanci taji yana nuqurqusarta. Ta sauke idanunta a nutse akan Akhnan,duk da zuciyarta ba digo na nutsuwa kwata kwata. Tayi niyyar barin Akhnan ta nesanta kanta da agadez.....don ta samu daman salwantar da rayuwarta.....amma a yanzun....ba zata yi hakan salin alin ba. Ya kirata da RED LINE din da ba'a qetarewa nasa......amma ita a yanzun zata qetare shi. Zata taka ta kuma turmurmusa wannan line din.....idan yaso taga mene zai aikata. "Lokaci yayi" Ya fada da wani faffadan murmushi.....murmushin da ba mammina kawai ba.....harma wanda yake nesa ya gani. Ta dauka da ita yake magana haka kai tsaye....lokacin me?,murmushin me yake?,abinda ya tunxurata kenan ta buda bakinta a tunzure. "Ku kamata!" Ta bada umarnin a hargitse sannan kuma a tsawace da sautin daya isa kunnen harna nesa ma. (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) Saidai kuma......taku d'aya tak sukayi aka ji karar sanda yana bugun qarfen bene daga bayan mutane na ciki dana waje. Sau daya. Sau biyu. Sau uku Kaf courtyard ya dauki shuru. A hankali.....da wani irin yanayi jama'a suka fara matsawa gefe. Guards suka juya. Dattawa suka miqe tsaye cikin firgici da wata irin dimautacciyar d'imuwa "BAZAI YUWU BA!" Wani dattijo ya furta kafatanin ilahirin jikinsa yana rawa kamar mazari. Qara bugun sandar ya sake bayarwa. Tak… Tak… Tak… Daga cikin taron mutanen.......wani dogon mutum cikin farar babbar alkyabba ya fara qarasowa. A hankali,da takun da kowa a Agadez ya sanshi. Mammina ta hade gira tana duban mutumim. "Wanne me tsaurin idanun ne wannan.....da zai keto tsakiyar mutane sannan ya iso nan ina tsaka da yanke hukunci?....ko kaima kazo hanani kai khadeeja muhammad hammud prison dinne?.....shin kazo dakatar da nine kamar yadda wancan malamin d'an gidan ibraheem yake yaudarar kansa da ganin zai iya?" Ta fada tana nuna haisam dake tsaye,tana jin kuma dole ta sake tsaurarawa. Dole ta saka tsoronta a zuciyar kowa. Da wani irin nutsuwa ya janye hular alkyabbar dake kansa. Gaba daya courtyard din ta daskare na wasu sakanni. Jinin dake yawo a jikkunan mutane da dama dake gurin ya nemi tsayawa cak. Wasu suka ja baya cikin tsoro. Wasu kuma suka durqusa suna jin kamar girman wannan almarar yafi qarfinsu......yafi qarfin abinda zasu iya jurewa. “SULTANE…” “…Sultane?!” “ALLAHU AKBAR!!!" Wasu muryoyin dake da sauran dakiyar zuciya suka rude da fada duk da akwai burbushin tsoro a tare dasu. Sultane ne......a raye......a tsaye......yana kuma duban mammin kai tsaye.....kamar ita kadai ce dan adam me numfashi a gurin. Da wani irin gigicewa da madaukakin tsoro taja baya. Gane gane ta fara yi ko jifa akayi mata?. Sultane ne dai.....sultane take gani,a raye.....a tsaye a gabanta cikin qoshin lafiya. Sultane dai da aka masa wanka a gabansu.....sultane dai da aka hada cikin likkafani......sultane dai da aka binne yau kwana daya daya kwana kusan talatin da takwas?. “…A’a.” mammina ta furta tana girgiza kai a rude gami da kallon hagunta da damanta waiko wani zai taimaka ya tasheta daga mummunan mafarkinta. "BAPPIIIIIIII!!!!" sunan da Akhnan keta qoqarin fada tun dazu.....sunan data furta shi a zuciyarta yafi sau d'ari.....ta kasa fada a fili amma a yanzu ya subuce ya fito daga bakinta. Har a yanzun......da yaji fitar sautin d'iyarsa.....diyarsa mafi soyuwa a garesa.....sosai dab da shi ta cikin kunnensa.......har yanzu sultane bai kalli kowa sai Mammina. Only Mammina!!!. Yana jin sanda Akhnan ta fada jikinsa da wani irin qarfin da sai da yasa dukka hannuwansa ya tallafeta a jikinsa,still idanunsa akan mammina. "Bappppp....." Saita kasa qarasawa idanunta kafe a kanshi. Numfashinta ya katse daga qirjinta......abinda ya sanya haisam saukowa daga gurin. Da wani irin sassarfa.....da wani irin zafin nama yana karbeta daga hannun sultane yana kiran sunanta a jejjere. Sakar masa ita yayi.....a hankali.....a tausashe.....da wani irin amincin daya tabbatar zai daidaita numfashinta a qirjinta....da yaqini da duka amannar data hanashi jin D'ar ko d'aya da suman da Akhnan ta tafi. Ba yaune karon farko data fara suma a hannunsa ba.....amma a yau din,sai yakejin kamar suman ya banbanta dana kullum. Sai yakejin wannan suman data tafi ta tafi kenan. "Akhnaaann" Ya sake kiran ta da gaske yana girgiza fuskarta a tafin hannunsa. Cak ya dauketa yana adanata a qirjinsa,sannan ya fara takawa da sassarfa yana fita da ita daga courtyard din,guards dinsa suna buda masa hanya kafin ya iso gurin,yayin da sultane ke tsaye gaban mammina.....ko na second daya ya gaza dauke idanunsa a kanta. *zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 08187255862 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 08187255862 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 123* ___________________________ https://chat.whatsapp.com/BkfPzSEDhnsIwyCD8LNGkm?s=cl&p=a&mlu=0 *IDAN KINSAN BA ORDER DIN KAYA ZAKI DINGA SAKAWA BA* *IDAN KINSAN BA BUSINESS KIKE DA NIYYAN YI NA KAWO KAYA DAGA CHINA BA KARKI SHIGA* *_DON ALLAH KARKI BATAWA KANKI LOKACI_* *_Assalamu alaikum my loyal people_* *_Barkanmu da wannan lokaci,kuma barkanmu da warhaka_* *_akwai da dama cikin mata wadanda suke sha'awar yin order kaya daga CHINA zuwa NIGERIA,NIJER,CAMERON,CHAD da GHANA_* *_Amma rashin samun amintaccen company....ko hannun wanda zasu dinga siyan kaya ta hannunsu cikin aminci ya hanasu_* *_To a yau addu'ar da yawa daga cikinku ta amsu,don nayo muku tsarabar kamfanin da zakuyi siyayya ta hannunsu su kuma dora muku kayanku har qasarku cikin aminci ba tare da fargaba ko d'ar d'ar ba_* *_kunsan komai nawa TASTED AND TRUSTED ne,to wannan kamfanin idan akwai abinda yafi TASTED AND TRUSTED ma shine_* *_Baki da fargaba kota sisin kwabo,ni SAFIYYA HUGUMA na tabbatar da hakan_* *_Zaki iya kasancewa dasu group nasu,inda a nan zaki hadu da agent dinsu da CEO nasu gaba daya ta wannan link din,zaki samu bayanansu da komai da ya shafi mu'amala dasu_* *INA ME BAKU TABBACIN AMINCI DA INGANCI DA SAUQIN MU'AMALA DASU DA IZININ ALLAH,BAN TALLATA MUKU SU BA SAI DANA GWADA* *Allah ya dafa mana,yasa mana albarka a nemanmu,ya albarkaci halal dinmu ameen summa amee* ___________________________ “Kin gama?” sultane ya fada da nutsuwa da wani ciwo cikin muryarsa. Soma girgiza kai ta farayi a gigice,wata maqurar gigicewa da bata taba yinta ba kaf rayuwarta. Karon farko ta rasa kalmomin da zatayi amfani dasu kaf rayuwarta don ta kare kanta. “Na baki shekaru maay kyau.....” muryarsa ta fita da nauyi “Na baki suna da kika riqa kike amfani dashi cikin izza da alfahari" “Na baki amana da nake zaton ko bayan raina ba zakici ba,ba zaki tozartar da ita ba.” Sai ya dan matsa kusa da ita. “Amma kina jiran mutuwata ne kawai ashe?." Ya fada idanunsa suna yin wani irin duhu. “…domin ki cinye iyalina?." Wani irin shuru nauyi ban tsoro da kuma ban mamaki ya cika gurin. Kowa ya kasa motsi,kowa ya gaza takawa daga inda yake,kowa ganin komai yake kaman shirin film ko cikin labaran hikaya. Wai matacce ya dawo.....ya kuma dawo a daidai gab'ar daya kamata dama ace ya dawo din. Ya dawo a sanda agadez ke dab da nutsewa. Ta cikin wannan shurun sautin kuka ke fita. Ta cikin wannan shurun sautin kukan mutane da dama ke fita. Banda falaak,falaak din data daskare tun sanda sultane ya shigo.....take zaune a gurin kamar wani gunki,kuma dai har yanzun a zaune take,amma amma unconscious. Idanunta da kunnuwa ne kawai suke aiki a jikinta.....banda wannan......ba wani abu dake aiki tattare da ita. Sake takawa yayi zuwa gabanta,idanunsa dauke da wani zuzzurfan kallo. Ba irin kallon mata da miji ba.....ba irin kallon dake dauke da taushi qauna ko bege ba.....aah.... Kallo ne da wanda akaci amana yakewa wanda yaci amanar tasa. Kallo ne irin na wanda soyayya ta juye masa zuwa zazzafar qiyayya. "Kinyi mamakin dawowata ko?" Ya fada yana sake jin wata matsananciyar qiyayyarta tana hudashi. "Ka saurareni!" Ta qwato kalaman da qyar tana jin yadda harshenta da maqoshinta gaba daya suka bushe,ba wani digon yawu,tana ji kuma a ranta da zuciyarta cewa.....komai bazai tafi a haka ba.....komai zai daidaita. Hargitsin na wani d'an lokaci ne kawai. "Shuru!" Ya fada cikin daka tsawar data sanya kowa sunkuyar da kansa cikin ladabi bawai iya mammina kawai ba. Sabon abune wanda basu taba ganin irinsa ba. Sultane yayi magana da hadimai da irin sigar nan bama ballantana kuma matarsa.....matar tasa ma kuma GIWA. "AKHNAN!" Ya kira sunanta a kausashe. "Yarinyace da aka rasa uwarta" Sai muryarsa ta karye. "Na dorata a hannunki" "Amma maimakon ki zame mata mafaka......sai kika mayar da rayuwarta filin yaqinki" Motsawa baya kadan mammina tayi,komai yana gwada mata duk abinda ke faruwar nan da gaske ne yake faruwar. "Kin rabata da danginta....." ".....kin cusa mata qiyayya" "Kinci amanar gidan nan" Ya dakata yana jan numfashi da qyar idanunsa suna sauya launi. ".....amma abinda yafi karyani....." ".....ashe duk tsahon shekarun nan jiran mutuwata kike ki tarwatsa iyalina....ki tarwatsa ahalina.....ki shafe komai nawa daga duniya". " Wallahi ina sonka" Ta fada tana girgiza kai,tana jin kamar kwanyarta na shirin fara aiki ba daidai ba. Ji yayi kaman ta dauki guduma ta doka masa a tsakiyar kansa. "Kina dai son nasara.....kinason nasararki,kuma kin shirya yinta ta kowacce hanya. Kansa ya dauke,don baya qaunar ganinta ko yaya,ya waiwaya ga tarin guard din dake tsaye. "Ku saki Ahmed.....ku fitomin da safiyyatah!.....sannan ku tabbatar.....duk wanda aka tsare bisa zalunci a sakeshi bisa yardar yarima haisam" Ya fada maganan da wani amo. "Kinsan me yasa ban bayyana tun farko ba?" Ya sake juyawa gareta sanda guard din ke fita da sassarfa don cika umarnin adalin sarkinsu. "Saboda inaso naga iya duhun da zuciyarki ke dashi.....a kwanciyar da nayi da sunan ciwo.....ba ciwo bane.....hutu ne da haisam ya yanke bawa gangar jikina.....na huta,na karanci wasu abubuwa da xirga zirgar mulki.....kula da jama'an dake wuyana......da makircin masu makirci da idanuwana basa iya gani....." ".....ina kwance.....amma ina iyaji.....ina kwance amma ina gani......naji!.....na gani....tun daga sanda kika fara saka guba cikin fankoki da ac da pillow din da zan dora kaina a kai......daga sannan haisam ya fara shirin yadda zan mutu a idanun duniya kafin ki sakani nayi mutuwar gaske." Wani irin shock ya sake shigan kowa. Mamakin wannan idea ta yarima sheikh muhammad haisam yana sake shigarsu. "Nasan wacece ke zaituna......gudajjiyar me laifi daga Ethiopia......wadda ta biyo safeena......ta biyo dukiyar ajani.....wadda ta shigo ahalina.....saidai wani abu daya...." Ya fada yana hadiye yawu da qyar. "Shi Allah......adalin sarki ne.....ya hanani sanin wacece ke......bayan inacan ina damuwa don baki haihu ba.....ashe ya hanani....bani kadai ba.....ya hanaki haihuwa da dukkan mazan da kika aura saboda bamu da haqqinki......saboda ke din GUBA ce.....saboda baki cancanci zama UWA BA!" "Ba hukuncin agadez kawai ke jiranki ba,.....zaki isa Ethiopia......zaki kuma amsa nasu tuhumar qarqashin jagoranci da binciken sheikh muhammad haisam" "Haisam kuma?" Ta fada tana dauke idanunta daga kan handcuffs din da ake maqala mata. Da farki kafin ya kira sunan haisam.....sanda ake maqala mata ankwar.....tana dubanta ne.....tana jin cewa itace mafi girman tozarci a gareta......amma yanzun da yake shaida mata cewa.....zata fuskanci tuhuma daga wajen hukumomin Ethiopia.....kuma qarqashin sheikh haisam......sai taji wannan tozarcin yafi na maqala mata handcuffs din sau dubun dubata. Bai amsa mata ba.....amma yaga meye cikin idanunta. Nadama yakeso ya gani me zurfi,duk da hakan bazai qaresu da komai ba shi da ita.....amma sai yake hangen akasin hakan daga idanunta. Kansa ya sake daukewa,sai ya waiwaya ga al'ummar dake gurin. "Ba ita kadai ba.....duk wanda ya taimaka wajen qulla dukkanin wannan sharrin......to xa'a bincikeshi shima". Ya juya yana nuna mammina da yatsarsa. "Amma ita......ta rasa matsayinta da komanta a wannan masarauta daga yau!". Daidai sanda guard din suka fara janta. Wani irin fusga me cike da rashin girmamawa. "Muhammad!!!......don Allah!!!.....ka tsaya ka saurareni!!!,sharrin maqiya ne.......abinda kazo yanzun ka tarar yana faruwa!....." (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) "Abinda ke faruwa yanzu?.....wansa ya faru a baya fa?.......ko alfashar da kikaso yi da hadiminki da kika saka aka qulle da sunan d'an tawaye saboda bai baki had'in kai ba shima yansu ya faru?!!!......zaituna!.....Ki kirani da matsayina.....ba da sunan mijin da kikaci amana ba....sunana na gaske yabar bakinki da bashi da tsarki!." Ya fadi yana jin zuciyarsa kamar zata tsinke daga qirjinsa ta fado. Dif wuta ta daukewa mammina.....bama ita kadai ba.....kowa dake gurin. "Ka yafemin" Ta fada wani irin kukan baqincikin tona mata asiri da rashin mafita da bata hango ba ya qwace mata. Idanunsa ya lumshe yana jin jininsa kamar gashi yana hawa. Ya lumshesu na second daya yana jin kamar ya binne wadancan shekarun gaba daya. "Da ace laifin a iya kaina ni kadai yake......" ".....wataqila na iya yafewa" Sai ya bude idanunsa da suka sauya zuwa kalar ja,wani yanayi daba wanda ya taba ganin sultane a cikinsa. Wani yanayi daya sanya kowa sadda kansa qasa. "Amma kin cutar da marayi.....ba daya ba ba biyu ba.....uku!.....dukka jinina.....akhnan.....mahmud.....da jinjirin ajani......kinso hada haramtaccen aure a tsakanin jini daya......saboda SAFEENA KAWAI?". Mummunar kaduwa ta sakeyi.....dukka wannan.....dama sauran sirrikanta......haisam ya sani?,haisam ya gaya masa?. "Ka yafemim....bazai sake faruwa ba.....ka dakatar dasu mu fahimci juna.....zan gyara kura kuraina.....zan gyara komai" Ta fada tana jin wata masifa da bala'i suna tsarga mata. Daga waje.....ta hangi tarin 'yan jaridu kafe da cameras da takardu abubuwan rubutu da abubuwan nadar sauti.....ta tabbatar kuma jiran fiddo da ita kawai suke.....kaman yadda kura ke jiran shigowar nama dakinta. Murmushi me ciwo.....shine abinda ya subucewa sultane....irin ciwon da wanda ke nesa ma sai daya hangoshi. Mamakin rashin kunyar mammina.....mamakin qarfin halinta. "Matata?" Ya tambaya kaman yana tantama. Ya daga idanunsa yana kallon dattawan da kyau. "A cikinku.....a nan na tabbatar akwai wadanda suka shaida daurin aurena da zaituna shekarun da suka wuce......to a yanzun a gabanku inaso ku shaida....." Sai ya kalli magatakarda. "Dakai da mataimakanka.....dukkaninku ku ukun ku rubuta.....ni muhammad hammud........sultane na agadez......na saki matata......" "Sultaaannne!!!......don Allah!!!!" Ta fada tana turjewa guard din sanda suke dab da fita kuma take jiyo kalaman bakinsa. Abu na qarshe da zai mata da yafi komai ciwo cikin abinda yayi ko yace kenan......ya rabata da aurensa....auren daya bata kariya......ya bata garkuwa......ya bata abubuwa da yawa da bata isa ta mallakeshi ba. Koda da amsa sunan MATARSA kawai wata alfarma da martaba ce a tattare da ita. "......na saki matata zaituna saki daya" ".......ya isa sultane.....don Allah!!!" Ta fada tana hada hannayenta biyu guri daya daga inda take tsaye. "Na saketa saki biyu" "Na roqeka sultane don Allah!!!" Ta sake fada da mahaukacin sautin daba wanda ya taba jinsa a tattare da ita. "Na saketa saki uku!" Ya qarasa fada da wani sauti da amon daya ratsa gurin,shuru kuma ya maye gurbinsa. "Ku ninke ku bata dukkanin takardun uku ta fita dasu......don wannan ce fitarta ta qarshe a gidan nan......" Ya fada cikin umarni. Sauri sauri suka ninke.....suka kuma miqawa guard din suka karbar mata. "A tabbatar a yau.....basai gobe ba.....an kwashe komai daya danganci zeenatu anbar gidan nan dashi" Yayi magana ta qarshe yana fita ta qofar baya,qaramar qofar daya shigo a dazu. Waiwayawa tayi tana duban tafisu. Ta yaya zata bari a tafi da ita haka a qasqance ba tare da tafisu ba?. Ta rasa kowa amma ba zata rasata ba....a duk inda zata fuskanci hukunci tasan zata taimaketa. "Tafisu.....tana daya daga cin...." "Karki kuskura ki qarasa" Tafisun ta fada tana dagawa mammina yatsa,abinda ya kusan sumar da ita kenan da wani irin d'an banzan mamaki. "Kin dauka nima shashace maciyar amana irinki?. Aduk shekarun da muka dauka....kin dauka ina aiki a qarashinki ne?,ina aiki saboda ke ne?" Ta mata tambayar data sanya mammina taji jinin jikinta yana qafewa. Kai ta girgiza tana dubanta idanunta fal da hawaye. "Ni 'yar halak ce.....ina zaune dake ne saboda AKHNAN......bazan taba manta halascin safeena a gareni ba...." Ta fadi muryarta tana katsewa da wani irin kuka me cin rai. "Mutuniyar kirki kenan...baiwar Allah....Allah ya rahmsheta" Sautikan mutane daban daban na yabon safeena ya dinga shiga kunneta. Da qarfi ta runtse idanunta,tana fatan ta daina jin wadannan muryoyin masu yabon safeena a gabanta. *zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 08187255862 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 08187255862 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 124* __________________________ *_Amintaccen gurin siyayya_* *_ingantattun kaya akan ingantaccen farashin da ba irinsa a kasuwa_* *_BONONZA DA PROMO akai akai_* *dukka sai a HUGUMA CLOSET* *Duniyar kayan yara,mata,maza,dukka* *shaddodi,atamfofi,laces,abayas,jakankuna,takalma,agogo,sarqoqi,English wears,night wears,under wears,da duk wani nau'in sutura babba da qarami* *_Karki yadda ayi babu ke.....leqa kiga yadda closet din HUGUMA kullum ke cike da kaya akan farashi me kama da KYAUTA_* *_YAN SARI....YAN REPOSTING.....DA SARAKAN ADO MASU SIYA DON KANSU....DUKKA INA MUKU MARABA_*🤝🤝🤝🤝 https://chat.whatsapp.com/FrqgC0YmUWP4FPmUzYuLJX ____________________________ "Na rayu ne saboda na bawa d'iyar safeena kariya daga dukka sharukanki....duk plan dinki da nake baki shawara....kin dauka ina baki shawarar ne saboda amfanin kanki?. Ko kadan,shawarata ina bayar da ita ne daidai da fitar gimbiya akhnan. Daidai da tafiye tafiye da nake yawan yi na kasuwanci.....ba kasuwanci nake zuwa ba.....ina zuwa ne takakkiya karbowa gimbiya akhnan tsari,rubutu magunguna da nake sanyawa a ruwan wankanta dana shanta,tun zamanin uwar hadima birra......har ita birra din ta gaji mahaifiyarta" . Kai tsaye sultane yake gyada kai,don kusan yasan komai,haisam kuma ya sake buda masa komai daga mutuwar da yayi yaje ya dawo,mutuwar da zai iya cewa ta kusan masa daidai da zuwansa lahira da dawowarsa. Daqyar yakai wadannan kwanakin,da qyar yayi surviving bai bayyana ba,saboda ya kasa taunawa......ya kasa hadiye abubuwan da idanunsa ke gane masa sam sam. "Tir dake...tir da halinki.....tir da daqiqiyar qwaqwalwarki.....na dade ina fargabar kada ki ganoni a shawarwarina......amma da yake makauniyar daqiqiya ce ke,wadda idanunta suka rufe a zalinci da daukan fansa,sai kika gaza gane komai" Idanunta ta runtse tana jin yadda ake yankar naman zuciyarta. Ita giwa......ita qanqantacciyar baiwa irin tafisu ke yankawa magana haka son ranta a bainar jama'a. Ta bude idanunta ta watsasu saman fuskar tafisu. Tana jin inama sultane ya mata lamuni,ya maidata ikonta koda na minti daya ne don kawai ta nunawa tafisu kurenta?. Saidai inaaaa....bakin alqalami ya riga ya bushe. Don takawa sultane yayi yana fita daga gurin gaba daya ma. Kamar kowa yana jira ya fitane,surutai na la'anta da Allah wadai suka fara tashi akan mammina dake tsaye a qofar qarshe tana kallon taku da ficewar sultane. "Ashe da bata zama ajalinsa ba,shi shine yake shirin zama ajalinta?" Ta tambayi kanta tana binsa da kallo,tsinuwar al'umma tana bin kunnuwanta zuwa kwanyarta,tsinuwa da la'anta mafi girma,wanda sai taji ta gwammace ta tunkari tambayoyin 'yan jarida akan jin tsinuwar talakawanta.....mutanen da suke rayuwa bisa umarninta da alfarmarta a baya. Ita. Sarauniyar da take bada umarni. Yanzu ana riqeta kamar mai laifi. Guards na Ethiopia na tsaye a gefenta. Ba girmamawa,ba tsoron nan nata da take gani a idanunsu.....ba ban girman nan wanda ke tattare da iko,aikinsu kawai suke kaman yadda suke serving kowanne me laifi. Babbar gate na masarautar suka nufa. Tafiyar da take jin kamar kowanne step na cire mata shekaru ne daga jikinta. Daya daga cikun guard ya tura qofar ya budeta,take kuwa Flashes. Cameras. Hayaniyar ‘yan jarida suka cika mata idanuwa da kunnuwa. Ta sake fidda idanunta tana mamakin cikar gurin. International press har da na qasarta Ethiopia da reporters dinsu kaca kaca......royal media.....da tarin mutanen da take tunanin ta wuce musu.....ta tsere musu yau gasu gata. Ko ba'a gaya mata ba,yanayin 'yan jaridar dake tsaye a gurin na qasashe daban daban dake zagaye da yankin sahel kawai ya gaya mata shiryayyen abu ne.....wannna abun....an shirya faruwarsa dama a yau din,bawai shi ya shirya kansa ba. "Ranki ya dade......da gaske ne cewa kin boye asalin identity dinki na asalin qasarki ta Ethiopia?" "Da gaske ne kin kubuta daga Ethiopia da sunan daba naki ba?" "Ranki ya dade.....me zakice game da zargin da ake miki wanda yake da alaqa da rayuwarki ta baya?" Kai kawai take girgizawa. Ba zargin ba.....ba mutanen ba ...tarin hasken cameras din dake shige mata idanu,yana kuma sake tabbatar mata da adadin yawan tulin 'yan jaridar dake gurin. "Sources claim your Agadez identity papers were false documents.” “Were you living under a fabricated royal identity all these years?” tambayoyi biyun da suka sake dimautata. Ta soma numfashi da qarfi. Saboda yanzu,abinda take tsoro fiye da prison ya same ta........public humiliation. Mutanen da take rainawa,take mulka,take tsoratarwa......yanzu suna kallonta cikin handcuffs,ana kuma tambayarta irin tambayar da akewa criminal sak!. Sai a yanzu ta fahimta.....shurunsa.....shurunsa da gaske hadari ne me girman gaske.....shurunsa yana gina rushewarta ne a hankali,cikin wani irin salo da bai buqaci gagggawa ba kwata kwata. Shurunsa!....da tasan yana da wannan ikon......tabbas data saka qaimi da kima sama da yadda ta saka a baya. Shurunsa!....inda tasan hakane.....da ta sanyashi ya zama me yawan motsi....me yawan magana a komai. "Are the accusations true?!” dan jaridan ya sake tambayarta da faransanci. "Did you manipulate the Agadez throne?!” "Do you regret what you did to the royal family?!”. Tambaya ta qarshe......tambayar qarshe data sanyata daga kai ta kalli dan jaridar "NADAMA" Kalma daya me dauke da haruffa shidda da ko bayan ranta batajin zata yarda ta rabi gawarta.....ballantana yanzun.....yanzun da har a sanda take tsaye a raye take. Ita kuwa ya za'ayi ta bari haisam yaga NADAMA a idanunta?. Ta FADI kenan fa?,shi kuma yaci nasara?. Janta da guards din sukayi zuwa gaba tare da datse 'yan jaridar da suka dauki hotunansu iya son ransu a mabanbantan yanayi shine ya katse tunanin ta,hotunan da suka zame mata abun tsoro.....hotunan da bata da tabbacin ina da ina zasu tsaya?. *H A I S A M* Cikin jikinsa yakejin wani yanayi na tashin hankali.......yana jin kamar a duniya bai taba jin tashin hankali irin wannan ba......irin yadda yaga akhnan shimfide a hannunsa cikin dogon suma.....dogon suman daya dinga jin kamar mutuwa zaiyi.....kamar binta zaiyi shima. Ya manta duk wani taimakon gaggawa daya iya.....da wanda aka koya masa na yadda zai kula da me yanayi irin wannan......kawai neman tallafin likita ta daban yake. Hannuwa da idanuwansa a kanta,sanda likitar ta gama bata duk taimakon daya dace. "Tana buqatar hutu da nutsuwa" Abinda tace masa kenan a taqaice. Idanunsa ya lumshe yana jin bayananta. Sai yaji kaman yayi tsuntsuwa shi da ita yaga sun bar agadez din. "Zata huta.... Lallai akhnan zata huta,alqawarin fansar raine wannan" Ya fada can qasan maqoshinsa ba tare da kowa yaji abinda ya fada din ba. Duk yaqin da yayi.....duk plan din daya gina.....bai taba tsoron rasa komai ba kamar yadda yake tsoron rasa numfashin akhnan. A hankali ya dora goshinsa saman nata,ya runtse idanunsa tightly. "Don't do this to me" Ya fada da wani irin rauni ganin ta dara mintunan da likitar tace mata zata farka. Muryarsa a wani irin karye. Kamar ba shine wanda ke tunkarar muggan masu laifi ba,ya kamesu daya bayan daya ba tare da tsoro ko shakka ba. Yau gashi a zube gaban mace.....cikin wani irin tarin rauni da tsoron rasata. Baisan baida juriya ba sai yanzu a kanta....baisan rago bane shi sai yanzu. "You scared me" Ya fada yana motsa wadannan labban nasa. "You weren’t supposed to carry this much pain.” ya fadi yana maida mata gashin kanta daya taba gefan fuskarta bayanta. "Not all at once" Ya qarasa fada muryarsa tana sakeyin laushi "I should’ve prepared you better.” ya fadi da zargin kansa cikin muryarsa. Sai ya sauke kansa kad'an. Karo na farko!.....karo ma farko bayan dogin lokaci ya bari gajiyarsa ta bayyana. ".....but i was selfish" Ya gayawa kansa yana jin dukkan tuhumar da zuciyarsa take masa daidai ne. "Ki yafemin......i just wanted it to end.” ya furta yana dora labbansa saman bayan hannunta. (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) Kamar taji wannan connection din......kamar taji wannan dumin.....kamar taji wannan lallausan labban da basa gajiya da narkar mata da zuciya da lausasan kalamai saita motsa yatsun nata. Daidai inda ya ajiye lips dinsa. Ta motsa kadan tana bude idanunta. Fes ta zubesu akan fuskarsa,komai yana dawo mata sabo daya bayan daya. Shi din dai......haisam dindai.....always him. Shi ta fara gani.....shi idanunta suka fara gani kafin kowa. "Haisamm" Ta kirashi da sunansa....sunansa din da sai yanzu ya soma sonsa tsahon lokaci....sunan da sai data fara furtashi sannan ya fara jin dadinsa.....sai da labbanta suka fara fidda sautinsa sannan ya gane yana daya daga cikin abubuwan da yakeso ashe a tattare dashi. "I'm here giiftii" Ya fada yana kamo fuskarta cikin tafukan hannayensa yana sanya idanunsa cikin nata. Yana kallon yadda numfashinta ya sauka. Ya sauka da wani irin relief. "I'm right here biftu" Ya sake fada ta sigar ra'da. Kallonsa itama take,tana qyaftawa a hankali,sai ruwan hawaye suka fara cika mata idanu. "Bappi.......he's alive" Idanunsa ya lumshe yana jin yadda take karya masa zuciya. "Yes giiftii" "......he's alive" Ya qarasa fada da taushi a muryarsa. Kuka sosai ta saki amma mara sauti,sai hawayenta......d'aya yana bin daya. "Ka sani.....na tabbatar ka san hakan tsahon wannan lokacin". Sake riqeta yayi sosai,yana sunkuyowa fuskarta da kyau. "“I needed to bring him back safely.” sai ya qarasa fadin. "And I needed Mammina exposed completely.” da wata irin murya cikin kunnenta,kamar ita daya kawai yakeso taji abinda yake fadi din. "Na dauka da gaske ya mutu.....na dauka mun binneshi" "I know.....i know habibti" Ta rufe idanunta tana kuka da wani irin rauni da taushi. Sai kawai ya kwanta kusa da ita kawai ba tare da ya matsa mata ba. Just enough for her to feel him there. Zuciyarsa na wani sake raunana,yana jin kamar baida kalaman da zai wanke kanshi a gurinta. "Sleep.....ki barci....ki huta.....everything is over now" Ya fada yana bata comfort sosai da duvet ta kowanne angle yadda zata jita safe yadda ya kamata. Shuru me hade da zubar hawayenta ya cakuda guri daya,bai matsa daga gurin ba,bai kuma daina jin yadda zuciyarta ke sauka ba a hankali. "Did you ever think I’d hate you for hiding it?” ta furta a hankali. Qasa ya danyi da kansa.....kalmar tana masa nauyi.....amma hakan bai hana boyayyen murmushi subuce masa ba,bai motsa ba koda yatsansa kuwa,sai tausasan labbansa daya motsa a hankali. "Yes" Amsar ta fita da dukkan gaskiyarsa. "And I was ready to live with that…” ya sake fadi. "…as long as you survived this.” ya fada da wata tarin nutsuwa data sanyayar da jikinta. *zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 08187255862 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 08187255862 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 125* ___________________________ https://chat.whatsapp.com/BkfPzSEDhnsIwyCD8LNGkm?s=cl&p=a&mlu=0 *IDAN KINSAN BA ORDER DIN KAYA ZAKI DINGA SAKAWA BA* *IDAN KINSAN BA BUSINESS KIKE DA NIYYAN YI NA KAWO KAYA DAGA CHINA BA KARKI SHIGA* *_DON ALLAH KARKI BATAWA KANKI LOKACI_* *_Assalamu alaikum my loyal people_* *_Barkanmu da wannan lokaci,kuma barkanmu da warhaka_* *_akwai da dama cikin mata wadanda suke sha'awar yin order kaya daga CHINA zuwa NIGERIA,NIJER,CAMERON,CHAD da GHANA_* *_Amma rashin samun amintaccen company....ko hannun wanda zasu dinga siyan kaya ta hannunsu cikin aminci ya hanasu_* *_To a yau addu'ar da yawa daga cikinku ta amsu,don nayo muku tsarabar kamfanin da zakuyi siyayya ta hannunsu su kuma dora muku kayanku har qasarku cikin aminci ba tare da fargaba ko d'ar d'ar ba_* *_kunsan komai nawa TASTED AND TRUSTED ne,to wannan kamfanin idan akwai abinda yafi TASTED AND TRUSTED ma shine_* *_Baki da fargaba kota sisin kwabo,ni SAFIYYA HUGUMA na tabbatar da hakan_* *_Zaki iya kasancewa dasu group nasu,inda a nan zaki hadu da agent dinsu da CEO nasu gaba daya ta wannan link din,zaki samu bayanansu da komai da ya shafi mu'amala dasu_* *INA ME BAKU TABBACIN AMINCI DA INGANCI DA SAUQIN MU'AMALA DASU DA IZININ ALLAH,BAN TALLATA MUKU SU BA SAI DANA GWADA* *Allah ya dafa mana,yasa mana albarka a nemanmu,ya albarkaci halal dinmu ameen summa ameen* ____________________________ Qarya take.....ta sani itama qarya take,a yanzun a duniya akwai wani abu da zai sanyata ta qishi?. Anya kuwa?,koda ranta ya dauka kuwa tunda har ya bawa sultane wata sabuwar rayuwa?. Ya fiddasu kuma daga makauniyar rayuwar da suke ciki. Bai barta ba bai kuma matsa mata ba.....amma da wani irin salo sai daya tabbatar ya sanyata bacci saboda zuciyarta ta huta,jikinta kuma ya karbi treatment din da aka bata. Ba bacci bane burinta ko muradinta ba.....muradinta taga sultane,amma sai gashi haisam din ya maidata duniyar baccin da bata shirya ba. ★★ Ta sake d'aga idanunta a hankali ta kalli babban royal agogon dake kafe a bango,kafin ta saukesu a nutse akan haisam. Haisam din dake zaune saman sofa.....gabansa table ne d'an madaidaici a ajiye,samansa kuma laptop ne wayoyinsa da tarin takardun da yaketa fama cikewa tun dazu. Idanunta suma sauka nutse akan fuskarsa,bata iya ganinta sosai,amma tar take ganin dogayen eyelashes dinsa da yake kallon takardun gabansa dasu,sai sukayi kaman sun hade da juna saboda tsahonsu,kamar kuma a lumshe idanun suke maimakon a hade. Juriyarta ce take qarewa......haqurinta yana gazawa tana dai daurewa ne kawai. Daga d'azu da abun ya faru har zuwa yanzu haisam ya hanata fita ko ina. Ya kira mata sultane ta wayar falaak ya saka ta a handfree,kuma sultane din ya gaya mata. "Ki zauna.....karki fita ko ina,har yanzu masarauta a hargitse take,zuwa dare....idan komai ya lafa zan shigo" Da wannan alqawarin na sultane.....da wannan idanun na haisam da yaketa tsareta dasu.....da nauyinsa na kalar hidimar da yaketayi da ita ya sanyata jan bakinta tayi shuru tana jiran lokacin da sultane yace zai shigo. Komai dare... Komai tsahon lokaci kuwa ba zata kwanta ba. Zata yita jiransa. Idanunsa ya daga a hankali sai suka hada idanu,ta janye kallonta daga kansa tana basarwa. Qarin hujjarsa......tana buqatar hutu,tana buqatar nutsuwa. doctors sun hana mata stress. Amma ita,tasan akwai wani abu daban. Tun safe yake fita yana dawowa. Long calls. Meetings. Guards daketa shigowa suna fita,duk da bata ganinsu amma tana jin motsinsu. Kuma duk lokacin data tambaya yaushe zata fita?. "Later" Kawai yake ce mata. Ya hana ta fita ko ina. Ya hana ta shiga council chamber. Ya hana kowa kawo mata details ya gargadi su birra sosai. Kamar yana kareta daga duniya. Ko yana boyeta daga dukkan komai. Yanzun daya kamata tana satar kallonshi,saita zame idanunta tana maidashi akan cup din tea din dake hannunta,wanda tuni cup tea din ya riga ya huce. Tana jin zurfin kallonsa a kanta,kallon da batasan yau adadin sau nawa ya mata shi ba. "You’re ignoring me again?” ya furta a hankali da wannan tarin calmness din nasa. Bata amsa ba,sai kawai ta shanye tea dinta a hankali,duk da ya riga yayi sanyi ba tare data kalli haisam din ba. Murmushi kadan ya saki.....wannan miskilancin ya motsa.....wannan izzar ta motsa......wannan jan ajin ya tashi wanda bayajin bayan mutuwa akwai wani abu da zai rabata dashi. "learned from the best.” Siririn murmushi ya subuce masa,ya ajiye file din hannunsa yana qare mata kallo a nutse,wannan jin kan nata yana burgeshi. Still taqi kallonsa,sai yaji kaman ana fusgarsa zuwa gareta,ya ture gami da tattara dukkanin takardun gabansa a hankali ya miqe ya isa gabanta,takunsa masu nauyi na amsawa cikin dakin. saidai akwai tazara daya bayar tsakaninsu. Ya sunkuya a hankali yana qoqarin kamo idanunta. Hanya qwara daya tak da zai karya alkadarin wannan rigimar. "habibti" Ya fada a tausashe har tana jin saukar muryar a kowanne sashe na jikinta,saidai still bata amsa ba "Kina fushi dani.....saboda naqi barinki fita waje?" Sai a sannan taso kallonsa amma ta kasa,hawaye ya taru a idanunta. Ta qagu ta sake ganin sultane,ta qagu,gani take kaman za'a sake ce mata ya sake mutuwa....gani take ban bada gaske bane shine. "Kaine ka kulleni a nan.....kowa yaga sultane ya qara.....kowa yana samun amsoshin abinda ke faruwa a cikin gida amma bandani". "Kina buqatar hutu" Ya motsa labbansa da wata kalar izzarsa daya saba da ita. "No....you needed control" Wani siririn murmushi ya bayyana a labbansa. "And if i did?" Ta zaro ido kafin ta narke fuska. "Haisam" Ta fada a shagwabe. Takowa ya sakeyi yana sake rage tazarar dake tsakaninsu. "Kin samu a hannuna....." "......You think I’d let you walk into another emotional storm immediately after that?” ya qarasa fada yana dage mata dukka girarsa biyun. Ta bude baki zatayi magana,amma sai kuma ta kasa. Cikin muryarsa akwai wani abu.....wani abu me nauyi dake bata tabbacin da dukkanin zuciyarsa yake magana. Idanunta ta sauke qasa a hankali. "Sultane nakeson gani...." "Zaki ganshi.....zaizo" "You keep deciding things for me.” "Only when I’m terrified of losing you.” Sai ya yi shiru na second biyu. Kamar yana tunanin wani abu na daban. Da alama har yanzu batasan girman matsayinta a zuciyarsa ba.....har yanzu....fake death na sultane ya karya wasu tsarukansa da yawa. Wasu shirye shiryensa. Ya shirya shayar da ita kalar soyayyar da ko cikin finafinai da litattafai bata taba cin karo da ita ba. A dubai......yaso kafa abubuwa da dama,yaso shirya abubuwa masu yawan gaske wannan issue din ya taso. (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) Zuciyarta ta buga da amsarsa daya bata. Duk lokacin da yake bud'e mata wani bangaren zuciyarsa,sai ta kasa ci gaba da fushi sosai dashi kaman yadda take tsarawa a bayan idanunsa. Ya bude lumsassun idanunsa a kanta,suka hada ido,wani irin shuru ya ratsa tsakaninsu,wadannan tsumammun idanun nasa.....a hankali suka sanya jikinta ya mutu. Wani irin tsumammen kallo,kamar ita kadai ce abinda yake iya gani a duniya. Ba zata iya jura ba,don haka ta janye idanun nata. Murmushi me sanyi ya kubce masa. "There she is" Ya fada da wani yanayi na tsokana a cikin muryarsa. "Who?" Ta tambaya da wani yanayi akan fuskarta. Takawa ya sakeyi yana hade tazarar dake tsakaninsu. Ya aza fuskarsa akan kafadarta,ya sanya bakinsa saitin kunnenta,muryarsa can qasan maqoshinsa da wani irin shauqi yace. "My stubborn wife" Kusan daukewa cak numfashinta yayi. Sai daga baya ta samu ta jashi da wani irin qarfi tana saukeshi a hankali,kafin tace ko shi yace komai aka sanarmusu "Sultane ya iso" Abinda ya sanyata miqewa cak kenan. Hannunta ya kama softly yana zaunar da ita. "Relax" Ya fada yana duban tsakiyar idanunta,saita dakata tana kallonsa har zuwa sanda ya ta ka ya bude qofa wa sultane. Daga bakin qofar bayyana.....yana tsaye kyam,wadannan kamannin nasa na cikakken ba'abzine tana bayyana. Giant tsaho da murjewar jikin da a yanzu akhnan taga kaman ya sake qiba ne,jikinsa ya sake yin kyau da murjewa,ya sakeyi fadi kamar wanda yaje hutu wani guri ya dawo. Shi daya ne.....shi kadai......yana me amsa sunan MAHAIFI bawai SARKI ba. Ba shigar sake nuna saraura ko mulki. Ba guard ko daya,hakanan ba komai sai farar jallabiyyar data nuna kyans,falaak na biye dashi qafa da qafa,kamar wadda akace mata itama zai sake ba'acewa rayuwarsu. Akhnan tayi sak tana dubansa,idanunta suka cika sosai da hawaye tana kallonsa "Zan iya shigowa?" Ya furta cikin salon neman izini,abinda ya azawa haisam kunyarsa. Girmansa yana sake qaruwa a idanunsa. Sarki ne.....amma yana neman izini ga d'iya da surukinsa. Baya haisam yaja,yana bashi hanya cikin girmamawa. Ya soma takowa a nutse idanunsa akan akhnan. Kasa jurewa tayi ya iso gareta,sai taji kaman yayi nisa tazarar dake tsakaninsu,ta miqe cak,ta kuma kwasa da wani irin gudu da ya sanya haisam sadda kansa,quruciyarta sosai tana bayyana. Juyawa haisam yayi ya soma takawa don ficewa da zummar basu space,saidai sultane dake rungume da akhnan a jikinsa bayan sun zauna ya dakatar dashi. "Koma ka zauna...". Dakin yayi shuru na wasu mintuna,bayan sultane ya kammala warware mata komai. Kuka take da wani irin laushi karyewar zuciya da nadamar irin rayuwarta ta baya. Tsanar mammina.....dama tsanar komai daya shafeta yana sake ratsata. Wanne abune yafi wannan ciwo da muni?,maqiyinka ya girmar dakai?,ya dinga bin rayuwarka yana rusata d'aya bayan daya?. Har yanzu zuciyarta bata gama amincewa da wai sultane bane raye a gabanta. Wani abu da tasan koda tafi kowa qaunar sultane a duk duniya ba zata sameshi ba,wato dawo dashi daga mutuwa,sai gashi wata babbar almara ta rayar dashi daga mutuwar da akewa shirin yiwa sadakar arba'in a jibi. Ta kasa d'auke idanunta a kansa......idan ta tuna duka abinda mammina tayi.....ta kuma juya ta kalli sultane dinta a raye.....sai taji komai yana kwaranyewa daga zuciyarta. "Ki yimin afuwa da barinki kika shiga wahala haka da yawa" Sultane ya fada cikin kulawa. Tabbas kowanne d'a da irin son da Allah ya azawa iyayensa a kansa,ita kam akhnan wannan tabbaci ne na cikin 'ya'yansa soyayyarta tafi ta kowa tasiri a ransa. "Kada kace haka bappi.....bansan me zan kwantata wannan yanayin ba......na binneka.....na soma koyon yadda zanyi rayuwa babu kai....sai kuma gaka?,me yafi wannan dadi a gurina." Murmushi ya saki,ya waiwaya yana duban falaak. Shigen abinda tace dashi kenan sanda ya zauna dasu bayan sakin morsa safiyya ta dawo gida. Morsa safiyyan da har yanzu ta kasa cewa komai. Shima ya hanata cewan,yace ta huta....ta huta daga dukkan abinda ta fuskanta. *zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 08187255862 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 08187255862 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽 💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 126* Bawai ta wahala bane.....hasalima kulawa ta musamman da kebantattun dakuna cikin estate guda da haisam ya ware yake ajiye duk wanda yaso daga cikin jama'ar dake da gaskiya da mammina ke kora a nan suke. Estate din da ya ajiye mutane masu yawan gaske,ciki harda su yalwan da yake jiran randa zaa wuce da mammina Ethiopia ya fitar dasu gaba daya suma. A ware masu gaskiya.....irin yalwa wadda amfani akayi da ita,ita kuma tayi amfani da son zuciyarta ta zauna da mammina din a matsayin uwar d'akinta. "Wait" Akhnan ta fada tana miqewa ta zauna sosai tana duban sultane din. Yadda tayin yaja hankulansu gaba daya. "Bappi.....waye ya shirya wannan fake death din?". Shuru sultane yayi na sakanni,sai kuma ya saki murmushi a hankali. Ya daga idanunsa a nutse yana duban haisam. Da sauri tabi kallon sultane din,sai nata idanun suka mata jagora zuwa ga haisam. Kansa ya kawar kad'an daga idanun akhnan din kamar wanda aka kama. "Kai?,kaine ko?" Ta fada fuskarta tana narkewa a kansa. Sultane dariya yayi,haisam na boye murmushinsa. Ya sani akwai abinda zai biyo baya duk ranar data karanci wannan gaskiyar. "Shi ya tsara komai.....the hiding place....devices da ake komai kamar ina gurin,koda tari ko motsi daga masarautata.....the timing,muhammad haisam.....the silent one......alsaamit" Idanu ta zaro a hankali,saita juya inda haisam ke zaune gaba daya tana kallonsa. "You!" "YOU DID THIS TO ME?" Ta tambayeshi tana sake shiga mamaki. Yadda ya gudanar da komai......yadda yayi kaman da gaske sultane ya mutu alhali yasan yana raye. Yadda darare da yawa ya hana idanunsa bacci saboda ya bata comfort na gangar jiki dana zuci. Yadda yayi haquri da komai daga gareta. Duka wannan?....duka wannan kuma bayan yasan sultane yana raye ne?. Ajiyar zuciya ya sauke quietly..... Already yasan wannan reaction din nata yana zuwa. Sunne kai kawai falaak keyi. Batasan sau nawa komai nasu zai dinga burgeta ba. Ita da maleek.....suna burge mutane da yawa......amma ita akhnan da haisam ne suke burgeta,duk da wanzuwarsu tare ba na wani lokaci me tsaho bane,amma ko na minti daya inde zasu kasance a guri daya sai taga wani abu daya tafi da ita. "Akhnan" Ya kirata da ainihin sunanta murya qasa qasa saboda sultane dake gurin. "No" Ta fada tana maqale kafada gami da d'aukan pillow ta jefa masa. Hannu yasa ya cafe.....wannan kallon tuhumar da take masa ya sanya ya kusa manta waye a gurin ya marairaice mata. Tari sultane ya danyi,wanda ke cakude da dariya,kusanma don ya boye dariyar tasa ya saki tarin kadan. "A idanunka na dinga kuka.....a idanunka na dinga jin zafin rasa sultane kana kallo......na suma duk don saboda kai?" Ta sake fada tana marairaicewa idanunta suna sake hada hawaye. "You knew every single thing!” "And you kept looking at me like nothing was happening!” ta qarashe fada da jefa masa harara. Sultane dai yana gefe......still yana qoqarin adana dariyarsa bayaso ta fito. Ya lura rigima ce take jinta sosai,wadda shikam bazai iya sasancinta ba,da alama tafi qarfinsa. "If I told you....." "I WOULD HAVE HELPED!” ta tari numfashinsa. Wani siririn murmushi ya subuce haisam din Shima. Rigimammiya ce ya sani......amma yau a gaban bappinta take gwada masa rigimarta ta farko. "That’s exactly why I couldn’t tell you.” "You can’t lie to save your life.” wannan karon daga falaak har sultane dariyarsu sai data fito. Juyawa akhnan tayi da ragowar hawayenta tana duban sultane da falaak. "Bappi....you're supporting him?" Ta tambaya da french. "I'm enjoying this" Ya fada abinsa a nutse. Juyawa tayi tana sake harara haisam,hararar da take qara mata kyau ita da blue eyes dinta gaba daya. "I was dying from grief!” “And you kept saying mysterious things like ‘trust me a little longer’!” MITA?. Ya tambayi kansa yana matse tasa dariyar,yaushe kuma ta koyi mita?. (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) "Giiftii....did you survive?" Ya tambaya a nutse,tambayar data saka falaak cusa kanta a pillow kaman wadda ta kwanta kawai,saidai dariyar ta take cinyewa. Baki akhnan ta bude cikin mamaki tana dubansa da idanunta dukka a waje. "That's not the point wallahi" Ta fada hawayenta suna gangarowa. Tuhumarsa take a baki.....amma kimarsa ce take ninkuwa a zuciyarta. Da qyar sultane ya saita dariyarsa. "Haisam...." Ya kirashi. "Ka cancanci fushin nan fa" "Na sani bappi.....na sani" Ya fada da sauri. Ta lura kaman shi da sultane abu daya ne.... Bakinsu daya,sai ta hade hannayenta a qirji tana duban haisam. “I’m not talking to you.” Sai ya d'an sunkuya kusa da ita. “You said that yesterday too.” yana jin kamar ana fusgarsa cikin wannan sabuwar character din tata. “And I mean it today.” “Habibti…” ya kirata. “If I could choose between you hating me…” “…or losing you to Mammina’s plans…” “…I would hide it all over again.” Kasa magana tayi,har na kusan second uku,saboda duk da haushinta— zuciyarta ta kasa qin fahimtar dalilinsa. Komai ya furta sai taji ya samu gurbi.....ya samu kyakkyawan muhalli a zuciyarta. Kauda kanta tayi.....tana pretending fushi dashi. “I’m still angry.” wani murmushi me cike da nutsuwa da kwanciyar hankali ya sauke. Ya sani.....komai da take pretending ne. Zuciyarta a tafin hannunsa take. Bayan a tafin hannun nasa ma......a bude kamar budadden faifai. Lokaci kawai yake jira isashe ya fara dura mata duk abinda yakeso.....ya sake maidata yadda yakeso ta kasance. “Good.” kawai yace,bayaso aci gaba.....zai iya sauka hanya a gaban bappinta. “What’s good about that?!” ta tambayeshi tana dan tsuke qaramin bakin nan nata. “It means you finally have the strength to fight with me again.” "Sai da safenku" Suka tsinci muryar falaak tana fada.....sai a sannan suka lura sultane ma shi tuni ya kusa bakin qofa abinsa. Kunya tadan kamasu.....amma sultane kamar baiga komai ba ya dakatar da haisam dake shirin masa rakiya. "Ka zunguro sama da kara.....ka koma ka kashe wannan sabuwar qurar data tashi kuma" Maganan ya sakashi sakin sassanyan murmushi,yayi qasa da kansa yana fadin. "A sauka lafiya" Ya maida qofar ya rufe yana durfafo akhnan din idanunsa a kanta,yanason tantance meye dalilin sabuwar rigima da sabuwar tsiwar data koyo?. ★★★Asubahin washegari......Sanda yake takowa a nutse zuwa dakin bayan fitowarsa daga sallar asuba. Sanye yake da baqar baqar silk throb data dace da hasken fatarnan tasa ta qabilar oromo,wani irin fari me kyan gani wanda ya cakuda da hutu da kula da kai da jikinsa da yakeyi. Itace abu na farko da idanunsa suka fara sauka akai bayan shigowarsa dakin. Tana zaune sosai saman green din abun sallah,kamar yadda tufafin jikinta suke da wannan kalar. Qur'ani ne riqe a hannunta,hasken safiya dake hudowa yana sauka a hankali saman fuskarta. Calmly ya zauna ba tare da yayi sallama ba ganin karatu take. Karon farko da ya fara jin sautin muryarta a fili cikin karatun qur'ani. "Ma sha Allah" Yake maimaitawa saboda yadda muryar ta masa dadi,da kuma yadda yaga dabi'unsa sun fara nasarta. Tana bacci ya fita,ya sanya mata alarm ne kawai,tun cikin dare suna tare da sultane anata shawarwari da qoqarin gyara b'arnar da mammina tayi. Takai ayar qarshe,idanunsa yana kanta,ta rufe qur'anin a hankali ta ajiyeshi. "Barka da asuba.....ina kwana" Ta hada dukka ta fada tana dubansa da idanuntan nan da suka rusuna suke nuna alamun bacci bai isheta ba. Bai amsa ba,saici gaba da yayi da kallonta. "You’re staring again.” ta fada da murmushi a fuskarta tana tuna daren jiya yadda ya gama rudata da saqonninsa ya kuma janye jikinsa ba tare daya mata komai ba. Karo na biyu kenan..... Abun sai taji kawai ya tsaye mata kadan a wuya.....zuciyarta kuma na zolayarta da YAUSHE KIKASAN DADINSA NE?. Saidai zancan gaskiya.....a jiyan abun ya tsaye mata sosai....ta zurma da yawa.....bata kuma zaci zai barta ba saboda yadda taga shima ya fita hayyacinsa. "You’re peaceful when you read Qur’an.” "I like watching that" Ya qarasa fada yana motsa labban nan nasa da suka fusgi hankalinta. Labban sa muddin zai azasu saman nata......sai taji komai na duniya yana kwance mata. Sauke idanunta tayi cikin wata siririyar kunya da yaga ta mata kyau sosai. Kaman ba ita bace a daren jiya ta nemi fita daga akhnan dinta ba zuwa cikakkiyar matar aure me buqatar kasancewa da mijinta ba. Saidai wannan little izzar ita ta taimaketa ta dawo saitinta. "Call birra.....ta taimaka miki kiyi packing abun buqatarki daya zama necessary ki dauka" Ya fada yana lumshe idanunsa a hankali. Yana tuna wayar da sukayi da nanay a daren jiya can cikin dare. Yau zata iso agadez.....zatazo taga safiyyanta. Ta gaya masa tunda aikinsa ya kammalu......tanaso taga safiyyanta kada taje ajali ya raba ganawarsu. Ta fada masa.....zasu taho da dukka yaran......balqess ce kawai ba zata samu zuwa ba.. Ta kuma sake gaya masa zasuyi daukan amarya ne.....zasu dauki akhnan idan sun gama kwanakinsu,zasu wuce da ita gidanta Kai tsaye idan suka sauka a jimma ta tare a can. Duk jikinsa yaji yayi laushi,shi bazai sake bari wani abu ya shiga tsakaninsa da matar sa har ya rabasu ba. A yanzu bayajin yana da wannan kunyar......wannan karar tasa dukka babu ita. Yana mazewa ne kawai bayason tabata a agadez.....kada ayi abun kunya.....amma yanzu da komai ya qare......yanaso ya nuna mata zahirin RAYUWA. Yanason ta sake sanin WAYESHI?. Yana kuma son idanunta su bude sosai. Yanason soyayya da matuqar qurewar da tun kafin yayi aure yakejin zai iya haqura da komai idan matarsa bata iya ba.....amma banda soyayya. Soyayya ta gaske.....bawai intimacy ba.....ba kwanciyar auren kawai da rungume rungume ba. Soyayya me dafa zuciya.....wadda ana iya rayuwa da abokin rayuwa da kowacce naqasa da sai samu. Saboda ZUCIYAR ta dahu da soyayyar...... ZUCIYAR kuma ita akeso. "Me yasa?" Ta tambayeshi a nutse. Kasa daurewa yayi,sai dayakai hannunsa ya shafi gefan fuskarta. "Because I’m taking my wife somewhere.” "Where?" Ta sake tambaya. *zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 08187255862 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 08187255862 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 127* ___________________________ *_Amintaccen gurin siyayya_* *_ingantattun kaya akan ingantaccen farashin da ba irinsa a kasuwa_* *_BONONZA DA PROMO akai akai_* *dukka sai a HUGUMA CLOSET* *Duniyar kayan yara,mata,maza,dukka* *shaddodi,atamfofi,laces,abayas,jakankuna,takalma,agogo,sarqoqi,English wears,night wears,under wears,da duk wani nau'in sutura babba da qarami* *_Karki yadda ayi babu ke.....leqa kiga yadda closet din HUGUMA kullum ke cike da kaya akan farashi me kama da KYAUTA_* *_YAN SARI....YAN REPOSTING.....DA SARAKAN ADO MASU SIYA DON KANSU....DUKKA INA MUKU MARABA_*🤝🤝🤝🤝 https://chat.whatsapp.com/FrqgC0YmUWP4FPmUzYuLJX ___________________________ "Madeena" Ya furta kalmar na fita daga anihin zuciyarsa da wani irin nauyi da kimar gurin dake qaruwa a ruhinsa kowacce rana. "Madeena" Ta fada itama idanunta a lumshe...... Karon farko da garin ya tsaye mata a rai da wata irin tarin soyayya.....shine tafiyar da sukayi shida ita. Sanda ta gane girma da matsayin gurin. A yanzu sake dawo mata garin yakeyi da wata doki kaman bata taba zuwa ba. "Eh can.....kina buqatar qarin nutsuwa,ni kuma......" Ya bude idanunsa sosai yana kullesu da nata. "…need to thank Allah for returning you to me whole.” wani irin taushi ya cika zuciyarta. Wani irin laushi sanyi qauna da soyayya. Sai taji kaman ya mata albishir na zuwa wani guri da bata taba zuwa ba. ★★Tana zaune daga bakin gadon,cikin wata nutsuwa,sanye royal abaya two in one data fidda sigar kanta da kuma jinin izzar dake jikinta. Wani irin kwantaccen kyau irin na asalin buzuwa. Saidai ita duka ba wannan take kalla ba. Haisam.....haisam dinta dake sanya da wata sassalkar throbe saqar qasar oman. Ta masa kyau,wani irin kwantaccen kyau me daukan hankali. Shi take kalla.....da wannan kyan nasa da wani lokaci yake sanyawa taji ta raina kanta da kanta idan har ta kalleshi. Links din hannunsa yake sanyawa a hankali,zara zaran eyelashes dinnan nasa sunwa idanunsa rumfa. Saita miqe a nutse,ya daga kansa zuwa gareta sanda yaji alamun tafiyarta yana sauke mata tattausan murmushi. Links din ta karba,ta fara saka masa a hankali,ya sauke wani tattausan murmushi yana jin dadin yadda tayi masan cikin kulawa. Idanunsa akan kyakkyawar innocent fuskar nan tata da tayi kusa dashi sosai. Ya miqa yatsansa a hankali ya aza saman tiny lips dinta dake tsananin burgeshi. Zagayasu ya fara yi da yatsan nasa,yana jin sulbinsu da taushinsu. Tadan motsa bakin kadan saboda wani irin yanayi yammm da yake saukar mata. "Ka duba kanka?" Ta tambaya da yanayin kulawa,saidai bata d'aga kanta ta kalleshi ba. Idanunsa ya fidda gaba daya alamun neman qarin bayani. "Tun safe kake pretending kana lafiya,amma zuciyarka bugawa take" Ta qarasa fadi bayan ta gama saka masa,ta kuma goye hannuwanta a qirji tana kallonsa,kyansa yana son bugar da ita. Yatsansa daya ya miqa ya kalaci hancinta. Ta tafi dashi ainun,duk da ba ma'abocin kallon mata bane shi.....amma yasan matarsa ta musamman ce. "Kina iya jinta yadda take bugawa yanzu?" Ya tambaya yana lumshe idanunsa da wannan murmushin dake qara masa kyau. Idanunta tayi rolling.....blue eyes dinnan dake tafi da nutsuwarsa. "Eh.....ba yanzu ba....ko yaushe ina iya jin yadda zuciyarka take bugawa". Taku biyu ya qara ta hade tazarar dake tsakaninsu,ta bude lallausan tafin hannuta ta dorashi saman qirjinsa. " Wannan gurin.....wannan muhallin....mallakata ce.....ta har abada.....zaka bani ni kadai?,zaka qyale gurin ya zamana baquncin soyayyata kadai ya taba karba?.....zaka ci gaba da mallaka min nan din har abada ni kadai?" Ta furta muryarta a sanyaye tana dora kanta saman qirjinsa. Murmushi ne kawai ke fita daga samam fuskarsa. Wani kalan murmushi da yaji zuciyarsa tana narkewa. A hakan da suke tsaye.....shima bugun zuciyarta yakeji,bugun zuciyar daya zamana cike da kishinsa. Fargaba taci gaba da mamayarta jin yayi shuru,amma sai taji tausasan hannuwansa yana dagata daga qirjinsa. Ya bude idanunsa sosai yana kullesu cikin nata. "Khadeeja" Ya fada yana motsa labbansa da suka bata sha'awa har suka sanyata rufe idanunta da kuma budesu. "Na'am". Kai ya girgiza. "Wallahi......bazan taba iya adalci tsakaninki da wata mace ba......ta yaya nasan ni rago ne?,bani da kalar wannan jarumtar zan bawa wata mace baquncin wannan gurin?. Gurin da ke kika fara budeshi sannan kece ta qarshe?. Kinsan yadda Allah ya jarabceni da sonki har kike tunanin zan iya naso wata macen kuwa?" Ya fada dukkanin idanuwansa da kalamansa suna fadin gaskiyar abinda ke cikin zuciyarsa. Kai ya sake girgizawa. "A cikin tarihin duniya.....banajin akwai namijin daya jarabtu da soyayyar wata d'iya mace.....irin yadda na jarabtu da taki khadeeja" Ya fada yana aza hannunsa saman qirjinsa,idanunsa sun lumshe kansu da budewa. Wani irin yanayi me sanyi.....wani irin yanayi me taushi taji yana ratsata. Ta bude idanunta a kansa har sau uku tana rufewa. Sai taji ta rasa a wacce duniya take?,ta buda bakinta a hankali zata sake magana,amma sai ya aza yatsansa akan lips dinta. (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) "Chapter closed please......wannan hirar batayimin ba.....muje ki rakani" Ya fada yana kama tsintsiyar hannunta. "Morsa......tasan sa khadeejanta zasu hadu kuwa?" Yayi tambayar wa akhnan sanda take tayashi saka bisht dinsa tana zagayawa ta bayansa tana gyara masa kafadun. Abinda ya sanyashi yaji kansa ya wani qara kumbura kenan. Tana treating nashi sometimes kamar wani sarki. Murmushi ya subucewa kyakkyawar fuskar akhnan. "Bata sani ba.....ta dauka kawai ordinary khadeeja ce zatazo" Murmushin gefan baki yayi a hankali "She’s going to cry.” "Both of them fa" Akhnan ta fadi tana sakin siririyar dariyar da taso shagaltar dashi,har baisan sanda ya saka hannu ya dawo da ita gabansa ba yana riqe da qugunta. Yayi missing dinta....kewa ta sosai,amma yaja jiki saboda yanaso taji a ranta she's ready......yanaso taji a ranta itama tanason mu'amalar......yanason kuma ya gane adadin matsayinsa a zuciyarta.....ya kuma gani....sannan ya gane din gaba daya. "And you.....you'll cry too?" Ya tambayeta bayan zubawa juna idanu da sukayi na wasu sakanni suna kallon junansu cike da shauqi. "I’m stronger than all of you.” ta fada idanunta suna rage girma a hankali da wani irin shauqinsa dake fusgarta. Tun daga saman kansa har tafin qafafunsa yaji wani abu ya yarfa masa. Sai ya sassauta riqon daya mata kadan,ya kuma sunkuyo saitin fuskarta sosai har tana jin wannan numfashin nasa me qamshin gaske dake fita zuwa saman fatar fuskarta. "Liar" Ya fada qasa qasa yana qaramar dariya. Sakin numfashi tayi cikin jin kunya,sannan ta tureshi baya a hankali da hannunta dukka biyun,amma ko gezau bai motsa ba ballantana ya matsa. Yana murmushi,idanunsa yana kanta,deep and soft. "You’ll stay with Safiyya and Falaak?” ta gyada kai a nutse. "We'll receive her here" Kai ya gyada a hankali yana zare jikinsa,taku biyu baya sannan ya juya a hankali. "Watch morsa safiyya carefully.....she may collapse from shock" Murmushi tayi har cikin ranta tana jin dadin yadda yake treating duk wani ahalin sultane. "You sound worried.” " Yes....I'm " Ya fada yana dawowa gabanta ya tsaya,ya bata lite kiss a goshinta,wanda har cikin jininta taji dumin lips dinsa. "Everything beautiful scares you first.” ta fada tana zura hannunta cikin nasa. "But somehow…” “…you still bring it into people’s lives.” Wani irin kallo ya mata......deep enough da ya sa zuciyarta bugawa. Sai ya kamo hannunta. Ya sumbaci bayan tafinta gently. "Pray for today" "I already did" Sai ya juya zai fita,don ya fahimci idan suna tare ita dashi basa gane muhimmanci komai sai kawunansu.....basa kuma gane yadda lokaci yake gudu sai sunyi da gaske. *zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 08187255862 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 08187255862 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽 Amma kafin ya kai qofa,khnan ta sake kiransa da wani irin laushi a muryarta. “Haisam.” Ya tsaya sannan ya waigo,sai ta zuba masa ido cikin wani irin softness. “Thank you…” ta dan dakata. “For bringing families back together.” shuru Na second biyu,kamar maganar ta tab'a wani very deep part a zuciyarsa. Sai ya gyada kansa a kadan yana duban blue eyes dinta dake jansa zuwa gareta. “See you soon, habibti.” ya furta da wannan husky voice din nasa,sannan ya fita ya barta da bugun zuciya mai laushi,da wani kalan murmushi a lips dinta,tare da jin cewa yau… zata shaida wata rana da baza’a taba mantawa da ita ba,sai taji kewa ta kamata....kewar mamminta. Inama ace tana raye?....inama ace harda ita za'ayi wannan kyakkyawan reunion din?. "Allahummagfir laha" Ta fada a hankali. Tun daga ranar data tsinceshi yana yiwa wasu lecture akan muhimmancin yiwa iyayen da suka rasu addu'a......bata sake bari rana ta fito ta fadi ba tare data saka a addu'arta ba. ★Koda kai baqo ne.....koda kuma kai din bakasan komai ba daga yanayin convoy na motocin dake bin kwalta cikin nutsuwa zuwa ainihin agadez palace zakasan cewa wasu mutane ne na musamman. Wasu baqi ne masu cike da daraja da kuma alfarma suka iso qasar agadez din. A daidai wannan lokacin morsa safiyya ke yafa mayafinta,abu na qarshe cikin adonta na yau. A shirye tsaf falaak ta turo qofa,ta dora idanunta a kanta a hankali tana kallonta. Tayi haske sosai da wani irin yanayi data tabbatar na shigar yaron ciki ne. Wani abu guda daya dake sanyata yawan sakin murmushi kenan,tana sake hamdala ga ubangiji dake daidaita komai cikin qaramin lokaci. A yanzun.....wannan fatanne cikin idanunta da zuciyarta......wannan burinne a ranta taga akhnan tana sauyawa irin haka,sauyin da zai tabbatar da shigar ciki a tare da ita. A ranar idan har ta tabbata......batasan wanne irin yanayi na farinciki zata shiga ba. Tana yatsina fuska ta qaraso. "Momma.....kin dade yau,suna kusa da titinnan fa?". Abun hannunta ta dauka tana sakawa. Abun hannun da kullum zata sakashi yana tuna mata da khadeeja ne da safeena. Ta sare zuwa yanzu da dukkan buri da fatan haduwarsu a gaba....saidai bata sani ba ko sai a rayuwa ta gaba?. "Bansan me ya sakani wannan nauyin ba falaak......yau fargaba naketa fama da ita." *zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 08187255862 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 08187255862 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 128* __________________________ https://chat.whatsapp.com/BkfPzSEDhnsIwyCD8LNGkm?s=cl&p=a&mlu=0 *IDAN KINSAN BA ORDER DIN KAYA ZAKI DINGA SAKAWA BA* *IDAN KINSAN BA BUSINESS KIKE DA NIYYAN YI NA KAWO KAYA DAGA CHINA BA KARKI SHIGA* *_DON ALLAH KARKI BATAWA KANKI LOKACI_* *_Assalamu alaikum my loyal people_* *_Barkanmu da wannan lokaci,kuma barkanmu da warhaka_* *_akwai da dama cikin mata wadanda suke sha'awar yin order kaya daga CHINA zuwa NIGERIA,NIJER,CAMERON,CHAD da GHANA_* *_Amma rashin samun amintaccen company....ko hannun wanda zasu dinga siyan kaya ta hannunsu cikin aminci ya hanasu_* *_To a yau addu'ar da yawa daga cikinku ta amsu,don nayo muku tsarabar kamfanin da zakuyi siyayya ta hannunsu su kuma dora muku kayanku har qasarku cikin aminci ba tare da fargaba ko d'ar d'ar ba_* *_kunsan komai nawa TASTED AND TRUSTED ne,to wannan kamfanin idan akwai abinda yafi TASTED AND TRUSTED ma shine_* *_Baki da fargaba kota sisin kwabo,ni SAFIYYA HUGUMA na tabbatar da hakan_* *_Zaki iya kasancewa dasu group nasu,inda a nan zaki hadu da agent dinsu da CEO nasu gaba daya ta wannan link din,zaki samu bayanansu da komai da ya shafi mu'amala dasu_* *INA ME BAKU TABBACIN AMINCI DA INGANCI DA SAUQIN MU'AMALA DASU DA IZININ ALLAH,BAN TALLATA MUKU SU BA SAI DANA GWADA* *Allah ya dafa mana,yasa mana albarka a nemanmu,ya albarkaci halal dinmu ameen summa amee* ___________________________ "Hmmm.....kin saka zancan ahmad dai a ranki....kin nunawa sultane kaman yadda yace kinfison d'anki a kanshi" Ta fada tana dariya. Dariyar itama momma tayi tana takawa zuwa hanyar waje falaak ta bita. Bawai bataso ahmad yaci gaba da sarautar agadez bane kaman yadda sultane suka yanke da haisam......aah gani take kaman yayi quruciya da yawa.....a qalla a barshi ya cika shekara ko talatinne zuwa da biyar. Amma a qarshe ita kanta taga ba wani zabin sama da wannan,don haka sai kawai ta bisu da addu'a. Daidai sanda take fitowa akhnan ta shigo cikin rakiyar hadimanta. Tayi kyau cikin wani tsadajjiyar atamfa exclusive wine colour da ratsin peach me haske. Wadda wuyanta da hannuwanta duka aka yiwa wani sirfani. Dan siriri ne na alfarma daga mafi tsadar zare. Tea boubou ce data zama kaman oversized a jikinta. Amma ko daga iya yadda dankwalin ya zauna mata a kanta.....sai tayi wani sirrintaccen kyau me jan hankali. A saman kanta kuma saman daurin kanta na ture kaga tsiya ta dora mayafinta,saita fita a matar aure da wani irin aura me jan hankali. Kaman yadda ta saba yanzu.....kanta tsaye ta isa jikin morsa safiyya ta rungumeta......itama saita rungumeta sosai tana jin wani farinciki yana mamayarta,kafin kuma ta zame a hankali tana gaidata,ta amsa mata tana riqo hannayenta,sannan ta riqeta suka fara takawa waje,daidai sanda hayaniya kadan ta qaru cikin gidan da motsin manyan qofofin gidan guards da securities. Sanda motocin suka tsaya cak a muhallin tsaiwar motoci na gidan....gurin ya cika da securities da guards na Ethiopia dana agadez gaba daya.....siririyar busar sarauta na tashi cikin wani yanayi da ba hayaniya a ciki....haka kawai sai morsa safiyya ta samu kanta da qarin faduwar gaba. Idanunta akan motocin sanda mutanen ciki suka fara fitowa,taga haisam ya fito,ya kuma zagaya side din motar daya fita a ciki zai bude,tabbacin mmamarsa ce a gurin,daidai sanda armelle ta qaraso tana mata magana akan kammala shirya dakin cin abincin,sai ta dauke idanunta tana maidawa ga armelle. "Sannunku da qoqari.....hakan yayi,kowa yana iya tafiya tunda an kammala k....." Ta qarasa maganan tana maida idanunta inda haisam ya fita dazu. Saidai kuma ta gaza qarasawa,saboda abinda idanunta ke gane mata. Wata razanniyar almara da Zuciyarta ba zata taba yarda da ita ba,don ta tabbatar idanunta ne suka yaudareta. Wata almara da taso tafi komai daga mata Hankali. Khadeejanta take gani,tana magana da wannan nutsuwar tata tunta quruciya,da wasu shekaru na girma,idanunta akan haisam.. Idanu ta zuba sosai,saidai fa suna sake matsowa tana sake ganin khadeeja dinta muraran a gabanta. "Itace.....Allah ita ce" Ta fada a fili ba tare data sani ba.....dukka ilahirin jikinta yana rawa,abinda ya sanya akhnan kama hannunta a nutse tana son bata nutsuwa,daidai sanda nanay ke janye idanunta daga haisam,wanda da alama wani bayani yake mata suka sauka akan morsa safiyya. Cak ta tsaya tana kallonta. Ta sani yaronta baya qarya....haisam a tsahon shekarun data rauneshi,tun daga quruciya zuwa girma ba zatace ga sanda ta kamashi da laifin qarya ba,amma kuma sai yanzu take sake tabbatar da maganarsa a zahiri. "Sadiyeee" Nanay ta faurta da murya me rawa. "Itace.....ta kirani da sunan da iya su biyu kadai suke kirana dashi" Ta fada a fili. Idanun morsa safiyya ne ya cika da hawaye,ta soma takawa da sassarfa tana fadin. "…Khadduu?” sunan saka nanay itama kasa jiran qarasowar morsa safiyya,saita soma takawa da nata hanzarin don ta cimmata. (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) A tsakiya suka hade ita da ita,suka yiwa junansu wata wawar runguma da saur kadan su zube qasa,saida hadimai suka lullubesu daga idanun mutane akhnan da falaak harma da haisam suka tsaya a gefansu. "Khadduu.....khadduu" Shine kawai abinda morsa safiyya ke maimaitawa tana jin kamar cikin mafarkanta take. "Sadiyeeee.....'yar uwata" Nanay ta furta da qyar saboda kalan kukan dake neman shaqeta. Sake rungume juna sukayi sosai,kamar masu tsoron idan suka saki juna d'aya zai bace ya sake barin dan uwansa. Suka raunana zuciyar kowa dake gurin,musamman sultane dake gefe tsaye shida motii da motarsu sai yanzu ta ida qarasowa. Falaak ta fara qwalla,saiga akhnan tana hawaye har suna fita a idanunta. Tana hango wannan tatacciyar soyayyar ta 'yan uwantaka har ina?. Inda ace mamminta tana nan yaya zai wannann kyakkyawar haduwar zata kasance?. Idanunta suka fada kan haisam,sai a sannan ta lura bai damu da kowa ba....ba wanda yake kalla a gurin sai ita,ita kadaice idanunsa suke kansa. Ido daya ya kanne mata yana hade yatsunsa biyu,ya mata maga da ido da yatsun ba tare da yace komai ba. "Kinyi kyau sosai.....karki kuka....zaki bata wannan fuskar". " Wannan mutumin" Ta fada cikin ranta tana gayyato jarumta. Batasan a wanne layi zata sakashi ba....a komai ya qware,komai kuma ya iya,ya isar mata da saqon soyayya cikin salo,ba tare da kowa dake zagaye dasu ya fahimta ba. Saida sultane da motii sukayi magana aka samu daidaituwar yanayin,suka fara takawa ciki hannuwansu cikin na juna,idanunsu cike da mamaki da qaunar junansu. "Kin tsufa.....girma yazo"nanay tace da morsa safiyya cikin murmushin da zai gaya maka akwai abinda ta tuna zamanin suna tare ta fadi haka. "Ke kuma har yanxu kina kuka idan kika tsorata" Dukkansu suka yi dariya cikin hawaye. Kasa jurewa morsa safiyya tayi,ta waiwaya tana duban haisam. "Kai ka dawomin da ita?ya akayi baka manta labarin khadduu dina ba saida ka dawomin da ita?" Tace da haisam dake musu gadi daga bayansu. Dariya kadan nanay ta sake cikin nishadi,duk da hawaye ne fal idanunta. "Danki ne fa......dankine da baki sani ba" Cak morsa safiyya ta dakata da tafiyar,ta juya gaba daya tana kallon haisam "La'ilaha illalllahu......muhammad?" Kasa qarasa magana tayi,har saida muryar sultane ta bayyana. "Idan safiyya ta gagara ci gaba da tafiya....to a nemo abun daukarta mana" Maganan ya bawa kusan kowa dariya a gurin. Anaani rumaisa noorah da khansaa gaba dayansu suna jinsu cikin wata sabuwar duniya,gasu a baquwar qasar da basu taba zuwanta ba. Wani irin zama ne akayishi cikin qawataccen parlor din na alfarma. Parlor ne da kusan sai manya manyan baqin sultane ko baqin da suka shafi cikin gidan ake saukarsu a ciki. Zama ne me tsayawa a zukata.....cike da farinciki da walwala. Dariya da murmushi na gasken gaske ba fake ba,wani irin nutsuwa me cike da sukuni da kuma walwala. Karbar baqin zuwa yanzu ya wuce hawaye da runguma kawai......ya kuma wuce zaman tattauna abubuwan da suka faru da sake bude tarihi tsakanin nanay da morsa safiyya,ya zarce ga zaman cin abinci na bai d'aya. Ba zancan surukuta a gurin nauyi ko jin kunya,motii nanay morsa safiyya da sultane sunaji a jikinsu dukkaninsu nasu ne. *zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 08187255862 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 08187255862 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 129* Saidai duk a wannan zaman....a wannan yanayin idanun akhnan lokaci lokaci yana fadawa kan dan matashin saurayin da batasan waye ba,wanda a qalla zaiyi sa'an hairaan ya girme mata sosai ko ba'a fada ba.....amma tana ganin kamannin mamminta a tattare dashi.. "Da jinjirin safeena daya bata fa" Maganan da yaja hankalin morsa safiyya,hannuwanta na rawa take riqe da Muhammad. Zaman cin abincin da bai yuwu ba,sai koke koke ya koma sabo. Akhnan jin Zuciyarta takeyi tana sake nisa da tsanar mammina sanda motii ya gama cikakken bayani shima muhammad ya dora da nasa,kafin motii ya sake karba. "Wannan zuciyar dukiyar ajani din.....ta muhammad ce....yamin wasiyyar ya barwa duk abinda safeena zata haifa,saboda yasan bai zarce kason daya zama haramun ka kyautar ba...kuma kaman yasan zai zamana baida kaso a dukiyarsa......muhammad yaqi karba.....yace na riqa masa.....ko na bawa obbo dinsa,shi kam yanzu neman ilimi zai tafi,kuma in sha Allah sati me zuwa zai wuce madeena can zaiyi dukkanin karatunsa,haisam ya gama masa komai lokacin tafiya kawai ya rage ". Data daga idanunta tana kallon haisam.....ba miji kawai ya gani ba. UBA ta gani.....wata KADARA ta gani me tsananin tsada da daraja. Wani LU'U LU'U da mallakarsa sai me tsananin sa'a. Ta sake maimaitawa kanta tambayar. "Wanne abun arziqi na taba yiwa Allah a duniya ya mallakamin wannan LU'U LU'UN?" tayi tambayar a hankali qasan ranta tana kallon shehnaz da tayi joining dinsu. Bata manta ba......a safiyar yau ya mata abinda ta kasa riqe kukanta. Ta samu labari dama daga birra.....kaf kayan da mammina ta dinga saidawa tana gwanjonsu ya maidosu. Secretly ya sanya mutanensa suka dinga shiga suna siyan kayan da farashin da yafi kowanne tsada da daraja. Komai ya maidashi a muhallinsa,kamar ba'a taba ba. Kwatsam sai ga takardar kamfaninta a hannunsa. Sahel couture.....kamfanin da mammina ta d'ai d'aita shi da mummunar sata......tare da hadin bakin ma'aikatan bogin data zuba a kowanne reshe na kamfanin,sannan kuma ta aza alhakin hakan akan aisa qarara. Ba kunyar nannie ba komai......taso ta mata tozarci,saidai bayan haisam ya maidata kamfanin bisa murde hukuncin mammina,ya dora aisa a wasu hanyoyi da dabarun da sai da suka gano daga inda komai ya fara. Ya barta taci gaba da rusa kamfanin har zuwa sanda tayi gwanjonsa. Ya ninka kudin ya kuma siya ta hannun jabeer ba tare da tasan waye ba. Saidai kuma.....a yanzun da takardun saheel couture yake dawowa hannunta da sunan mallakinta a karo na biyu.....ba sahel couture take gani ba. Wani gingimemen kamfani take gani,wanda yake da qarfin jarin da zai iya gogayya da sauran kamfanunuwan qasar waje. Sun mallaki komai nasu na qashin kansu,ba buqatar zuba hannun jari daga kowa. Sahel couture din daya zama wani na duniya gaba daya....ya fara qoqarin gina reshe a dubai,kusa da kamfanin turaren daya mallaka mata. Kamfanin turaren da har yanzu ta gasgata yarda ya zama nata. Saboda duk sanda suka zauna ita dashi......yanaso ya qarasa handling komai na kamfanin.....ya buda mata komai a matsayinta na CEO....mamallakiyar kamfanin sai ta kasa qarasa zaman dashi. Kudaden da take gani yana lissafi kawai akai suna gigitata tare da gaya mata anya reality ake magana?. Bai wani yarda ta masa godiya ko daya ba.....hasalima ya b'uge da tsokanarta ne. Tayi kuka sosai tana tuna ranakun baya data rainashi. A yanxun kuma da yake dawo mata da danginta daya bayan d'aya. Yake dawo mata da ahalinta.... Ruhinta farincikinta dukka tattare da ita saita rasa dame ya dace ta saka masa?. "Ya dawo mata da morsa safiyya.....jajirtacciyar uwar dataso rasawa.....ahmad.....ga muhammad da kwata kwata duniyarta batasan dashi ba sai yanzu. Ya qara kusanto mata da nanay....amintacciyar mahaifiyarta.....ya sake qara mata yawan 'yan uwa ta hanyar hada nasabarta dasu Anaani.....rumaisa.....noorah.....Aareef.....hussam.....balqees da khansaaa duka. Idan ta juya ta kalli Ahmad......ta kalli muhammad..... Sai taji wani abu me laushi da nauyi saman zuciyarta. Ashe dai itama tana da gata?,ashe 'yar gata ce itama sama da qasa,yayyen nan maza da take ganin wasu dasu.....ashe dai itama tana dasu?. Wata qauna lokaci guda irin ta 'yan uwantaka ta soma tasiri tsakaninsu,amma duk da haka sai taga kamar falaak ma ta fita murna da d'oki. Don ita din,bata da saurin sabo,uwa uba wannan dabi'ar miskilancin har yanxu bata barta ba. Daga baya mazan motii sultane ahmad muhammad hussam Aareef da haisam suka wuce sukabar iya matan. Su dai su akhnan suna zaune suna kallon ikon Allah. Lokaci lokaci sai nanay ko morsa su kalli juna,su saki murmushi,kosu riqe hannun juna. Sun manta dasu dake gurinma kwata kwata. Sabuwar 'yan uwantaka....tsohuwar soyayya,dangantar zuci ta fara motsawa. Hirarsu suke suna tuna baya,suna tuna daa....amma kuma idan suka tuna da safeena ako wanne gurbi saisun tsaya sun zubda hawaye. Anaani da noorah da kuma hasnaa sun wuce sashe na musamman dake manne dana nanay na baqi na musamman,amma rumaisa ta wuce kitchen inda 'yan aikin morsa safiyya ke qoqarin sake dora wani abun,duka cikin nuna girmamawa da karramawa ga baqin nasu. Yadda suke tuna safeena da yawan kukan da taga sunayi ya sake karya mata zuciya. Sai kawai ta miqe. Bata gaji da ganinsu haka a tare ba.......tana jin kamar mamminta itace ta ukunsu,tana tare dasu a sannan,don haka saita yanke bin rumaisa kitchen. Wani abu daya data lura dashi.....mulkinsu ko sarauta da yawan dukiya da iyayensu dasu kansu suka mallaka bata sanya sun rasa kansu cikin masu jin izza ko girman kai ba. Tana mamaki zamanta a Ethiopia yadda zata samu rumaisa a kitchen,duk da tarin hadimai dake qarqashinta wadanda aka ajiyesu kawai donsu hidimta mata. Ko yanzu data shiga,ta sameta ita da me aikin morsa safiyya guda daya......wadda asalinta 'yar oromo ce. Tana hada wani abinci rumaisa na gefanta tana kalla suna hira. Yadda taga rumaisa ta zage tana tayata hadawa,kawai saita samu kanta da sha'awar zama kamar haka. Falaak ta iya komai.....itama dai kamar su rumaisa din,ita aka baro a baya. Morsa safiyya ta taba fadi,duk daba da ita take ba,amma a sannan ta riqe abun,hartana jin zafinta tana ganin da ita take. Fada takewa falaak a wani yammaci datayi kuskuren hada mata wani abincin gargajiya na abzinawa. "Macen da bata iya girki ba ta rako mata duniya ne. Koda mahaifinta waye......samun hanya ko qofar zuciyar d'a namiji.....tana ga cikinsa,wato abincinsa." Burinta a yanzun daya ne tak!....ta zama cikakkiyar macen da zata hidimtawa mijinta ba....ba wadda bayi zasuyi hidima da ita sannan suyi da mijinta ba. Sai ta samu kanta dayin tattaki tana harhada plates din da aka gama amfani dasu. Daga me aikin har rumaisa sunso hanata amma taqi. Suka dinga juyawa time to time suna kallonta,har me aikin ta gama tabar musu kitchen din,saiga Aanani tana santin agadez,harta sauya kayanta zuwa na lounge wear,masu kyan gaske da taushi irin wanda safiyya huguma ke kawosu,saqar qasar china da kaloli masu kyan gaske. 08187255862. A sannan akhnan din ta nade hannun rigarta,dankwalinta ya zame tana son koyon yadda ake kwaba wani abincin fulawa. Rumaisa tana ta dariya,saidai kuma tana mamakin yadda lokaci daya ta canza. "Wallahi ni kam ba ruwana.....idan obbo yazo ya tarar kin manta dashi". "She already did" Wannan muryar tasa me taushi da nauyi ta bayyana. Cikin shakkarsa suka waiwayo,kowacce tana kallonsa tana qoqarin kama kanta,yayin dashi kuma dukka idanunsa suke kan akhnan. Muryar ta isa ga kowanne sashe na jikinta,sanda ta waiwayo kuma mamaki ya cikata. Yana sanye da All black pyjama da suka fidda sirrin kyansa. Wato a yau ya amsa cikakken sunan d'an morsa safiyya,shi yasa kanshi tsaye yake takowa har kitchen dinta?. Ba kunya.......ba nauyi?.....ba iso?. "Allah ya fara kishi.....bari na gudu" Rumaisa ta fada can qasa tana radawa akhnan,saita tsame hannunta daga kwabin,ta isa famfon sink kafin ya qaraso ta wanke hannayenta ta lalubi qofa. "Tsayani mana yaa rumaisa" Anaani ta fada itama da wannam tsoron nasa da rashin son wargin da suka sanshi da shi tana bin bayan rumaisa din salin alin.💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 130* Wani irin emotion ne,dake fusgar zuciya da gangar jiki zuwa ga 'yar uwarta......zuwa ga d'aya b'arin nata.....zuwa ga abinda zuciyar da gangar jikin sukeso. Tana ta kwab'a fulawar.....taqi kuma juyowa gareshi,saidai dukkanin gangar jikinta... Dukkanin wani bugu na zuciyarta.... Duk wani sashe dake gangar jikinta jiran isowarsa yakeyi. Shima kamar ita.... Idanunsa duka yana kanta,yana takawa da wani nannuyan yanayi na kewa,kamar ya shekara bai ganta ba. Saidai shi din yana qoqarin karantarta ne,tun daga tsaiwarta,ya zubawa bayanta idanu sosai. Idonsa ya lumshe yana fidda wani siririn numfashi. Boubou ce a jikinta,gashin nan nata me tsaho da santsi yasauka har kusa da mazaunanta,mazaunan da duk da cewa cikin sakakkiyar sutura suke......amma hakan bai hana bayyanarsu da bayyanar shape dinsu ba da tudunsu. Ya hadiye yawu a hankali yana jin wani irin mahaukacin kishinta. A tausashe ya isa bayanta yana karantar yadda ta qagu ya iso garetan,amma wannan izzar tata tana hanata nunawa. Baiga laifinta ba.....bazai kuma rabata da izzarta ba,don izzar na daya daga cikin abinda ya dauki hankalinsa da ita,yake kuma kan daukar hankalin nasa.(koda kun dade da miji.....ki zama me kamun kai da izza,bawai izza na girman kai wajen kyautata masa da biyayya ba.....aah....izza na kamun kai da nutsuwa,ba baragada......ki zauna kin b'andashe cinya da jiki,waike an zama d'aya,kai a wargatse ba kintsi,da wata bulalliyar rigarki wai ta zaman gida ce,tafi dadin sawa bata da nauyi. Ki zauna da daurin qirji koda datti wai ai wanka zaki shiga yanxu. Kai a tsaitsaye sai kice wai kitso kiketaso kije kin kasa.......please ki zama me aji,harshi kansa mijin yasan ke me aji ce,bawai yammatansu na waje ne kadai zasu zama hakan ba. Sometimes ma fa daidai da kiranki idan yayi kina iya ja masa aji,phone call,kina gani kidan basar ko sai ta kusa tsinkewa da sauransu,normally maza irin wannan attitude din yana jan hankalinsu sosai. Ba always available ba. Ya fita kullum kina hanyar kiransa,baisan ya kiraki ba. Wataran ki kama kanki,ki barshi ya kiraki da kansa mana,ire iren wadannan suna da alfanu sosai,amma hakan kada ya hanaki yi masa biyayya kyautata masa da faranta masa.......amma ki koyi jan class koda time to time ne). Cikin faffadan qirjinsa ya adanata yana mannewa da bayanta,ya sanya hannuwansa yana lanqwaso hannuwanta sake cikin flour din ba tare daya damu zata bata masa jiki ba,ya aza kansa saman kafadarta yana sauke mata wani irin numfashi me nauyi. "Haisammm manaaa" Ta fada a shagwabe tana qoqarin zame hannunta don kada ta b'atashi. Sai ya sake mata hannun,amma kuma ya musu kyakkyawan masauki saman qirjinta yana musu kyakkyawan riqon daya sanya jikinta duka ya hau rawa. "I’m jealous of anyone who makes you forget I exist.” ya fada da wani yanayi cikin muryarsa yana lumshe idonsa,har yanzu kansa yana kafadarta. "Come" Ya fada da wani irin energy yana sakinta,sannna yasa dukka hannuwansa biyu ya juyo da kafadunta tana facing nasa,sai kuma ya sake boyeta cikin jikinsa yana mata kyakkyawar runguma. "Mmnnn" "Mnnn" Yake fada yana sansansa kowanne lungu da saqo na jikinta dake bada wani kalar qamshi na daban. Wuyanta.....tsakanin dukiyar fulaninta.....cikin gashinta.......qasan hannunta......har fuskarta. Dariya.....itace ta qwace mata,dariyar da bata shiryawa ba. Don tana tsaye ne a tsorace,tana tsoron kada wani wanda zasuji kunyarsa ya shigo ya samesu a haka,amma shikam ta lura very comfortable yake abinsa. "Fuskata ma qamshin take?" Ta tambayeshi tana ware ido sanda ya hade fuskokin nasu guri guda. "Ko ina my wife.....ko ina da ina.....ba qamshi kawai ba....wani sulbi jikinki yakeyi.....kaman nanay ta canza miki soap ko?" Ya fada da muryar rada yana manne hancinsa saman nata. Kai ta daga a hankali. Yana noticing nata sosai,ko yaya wani abu ya sauya tattare da ita. Yana noticing cikin qauna da kulawa. "Wanne ne?,ya sunansa?" Ya fada yana cusa kansa cikin wuyanta yana sake jin laushi da dumin fatar gurin,gami da sassanyan qamshin da take fiddawa na cakudaddu kuma hadaddun turarukan shuwa incense and more(+234 704 229 3387) Wadanda zuwa yanzu suka fara guda jikinta sosai,kabbasarta kuma suka mannewa duk kayan da zata d'aga(iya wuya kina mace?,karki rabu da kabbasa)🫶🏽. "Sabulun......Mg's special soap (0806 2991549)......complete package ne na gyaran jiki......morsa safiyya tasa aka kawomin daga nigeria" Ta bashi details din muryarta a rarrabe saboda yadda dumin numfashinsa yake saukar mata da kasala. "A sake kawowa......dukka packages din.....fatarki......ta sake santsi......don Allah......" Ya kasa qarasa fada,sai wani wawan riqo daya mata yana matseta da kyau cikin jikinsa. "Haisammmm" "Say it again.......giiftii" Ya fada sunan yana ratsa kwanyarshi. Da gaske yake.....bayaso ta sauya masa suna......da gaske yake mata da yace sunan na masa tasiri. Idan ta kirashi da sunan,sai yaji kaman duk duniya ba wada ya kaishi sa'ar suna. "Please mana" Ta fada tana qoqarin tureshi a jikinta. "Kowa fa zai iya shigowa" Ta fada tana ture kanshi da gaske. Baya kadan yaja......ya kuma daga fuskarsa daga saman qirjinta daya cusa kai yana duban tsakiyar qwayar idanunta. Kallo daya tak ta masa ta kasa ci gaba. Ta janye idanunta da sauri gabanta yana faduwa. Wani irin kallo daya aje mata....wani irin sauyawa da kalar idanunsa sukayi ya sakata taji kaman zata birkice. "Don't do it again" Ya fada da muryar gargad'i "Haka kawai suka riqemin mata.....right?.... Nisa'ukum harsul lakum fa'atu harsakum anna shi'itum.... Matanku gonankinku ne......saina kasa zuwa ma gonata?. At any time?......idan sun gani.....next time su dinga turamin ke da wuri" Ya fada yana sake jawota cikin jikinsa da wani irin zafin nama. Sau biyu tana jin motsi ana kuma fita.....ta riga ta saddaqar akwai wadanda suka shigo.....kuma suka gansu a haka,dole ta saddaqar ta kuma sake masa jikinta kawai. Sai da yayi mai isarsa.......sai daya rage zafi sosai.....har tana jin yadda yake sauke numfashi a wahalce sannan yaja da baya. Kitchen cabinet din kawai ya dafe da hannuwansa yana sauke wahalallen numfashi,idanunsa akanta sanda take sulalewa zuwa saman kujerun island din kitchen din,saboda yadda taji qafafunta ba zasu iya daukarta ba. Ya jima a haka kafin ya isa gaban freezer,ya bude ya ciro ruwan gora me sanyi,fari qal dashi har yana zufa ya balle!murfin ya kafa kai yana kwankwada. Sai daya shanyeshi tas ya cilla roban cikin dustbin yana aje idanunsa a kanta. Abinda bata taba gani ba.....shan ruwan sanyi a tattare dashi. Ya zuba mata idanu a inda take cure tana qoqarin daidaita numfashinta. "Come" Ya sake fada da laushi sosai a muryarsa yana miqa mata hannuwansa. Da wani irin kasala da kunya take takowa gabansa,ya zuba mata dukkanin idanunsa yana kallon salon tafiyar me burgewa. Irin tafiyar da a gurinta kadai yake ganinta.....irin tafiyar da tasha banban da tarin mata. Izza.....da qasaita da wani irin yauqi a tattare da ita,da wani yanayi me jan hankali d'a namiji. Jikinsa ya sake riqeta da kyau,saidai a yanzun yabar qaramar tazara tsakaninsu,yadda zaifi jin dadin kallon cute face dinta. "Karki sake yin nisa dani please.....bazan iya jurewa irin wadannan dogayen awannin ba tare da ke ba". Idanunta ta lumshe,kalamansa suna sake dilmiyar da ita sosai. " Haisammm" Ta kirashi kaman yadda tasan yana so. "Awanni kadan ne fa" Ta fada softly tana duban cikin qwayar idanunsa. Sai daya rusunar da idanunsa sosai a kanta sannan ya amsa mata. "To you....awanni kadanne" Ya fada yana matsa hannunta cikin taushi. "Amma ni.....daidai suke da wasu darare da yininka masu tsahon gaske" Murmushi me taushi daya sanya dukkan kyawunta fitowa ta saki. "You're dramatic malam" "No.....I'm attached to you" Ta sauke idanunta cikin kunya. Sai ya daga habarta gently. Ya tilasta mata kallonsa. “Look at me.” ya fada da taushi. Ta dago idanunta gare shi. Zuciyarta ta sake bugawa saboda yadda yake kallonta da narkakkun idanun nan nasa masu nauyin gaske kamar wanda ya shekara yana nemanta ba tare daya ganta ba. Ya motsa labbansa.....wadannan kyawawan labban nasa masu taushin da bata iya mancewa da presence dinsu akan nata labban. “When you laugh somewhere else…” “…I want to hear it.” “When you smile…” “…I want it facing me.” “And when you disappear for hours.....” “…the palace stops feeling right.” kasa magana akhnan tayi har na wasu sakanni. Gaskiyar dukka kalamansa take gani a cikin idanunsa. Hannunta ta dauka ta dora tafin hannun nata a saman qirjinsa. “You really missed me that much?” ta furta da muryar rada,kamar bataso kowa yaji kalaman bakinta saishi. Qasaitaccen murmushin nan nasa na gefan baki ya saki a hankali. “I always miss you more than I should.” Kitchen d'in ya yi shiru,sai numfashinsu kawai. Sai ya jawota gently zuwa jikinsa. Ya rungumeta tightly. “Promise me something.” ya fada yana tura yatsunsa cikin gashinta daya tsone masa idanu me santsi sosai. “What?” akhnan ta tambaya. Sai ya rufe idanunsa na sakanni kafin ya budesu.💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 131* “Ko duniya ta cika dake da mutane da farin ciki…” “…ki dinga dawowa gareni.” “Always.” ya qarasa fada yana lowering voice nashi sosai. Hawaye masu sanyi suka taru a idanunta. Yadda yake mata magana sake dulmiyata yakeyin cikin matsananciyar qaunar da bata da suna. Yana kuma sake karya mata duk wani qarfi da ta mallaka a z uciyarta da gangar jikinta. Sai ta gyada kai a hankali. “I’ll always come back to you.” ta sake fada da wannan muryar me sanyi da rashin hayaniya. Goshinta ya sumbata da wani irin taushi. Wani irin relief ya sauka a idanunsa. “Good.” “Because I don’t think my heart knows how to survive your absence anymore.” cusa kanta tayi a qirjinsa,ya riqeta yana murmushi wani boyayyen murmushi,sannan ya soma takawa da ita ta qofar baya suna ficewa. ★Jet dinsu ya bar sararin Agadez ne cikin dare. Kasan hamadar na nisa a qarqashinsu.......yayin da city lights ke raguwa a hankali. A cikin private cabin din,komai na sauke da luxury mai nutsuwa,wanda suke qarawa akhnan jin wata sabuwar rayuwa tattare da haisam din. Duk sanda ta daga idanunta mutum biyu take gani. Wannan malamin da duniya ta sanshi a malami.....malami kawai makarancin alqur'ani masanin litattatafai......amma kuma a yanzu haka a gabanta......wata fuska tasa da mutane da yawa basu sani ba.....boyayyen billionaire..... Mamallakin madafun iko da kadarori. Baya ga turare.....da boyayyen harkar gold dinsa da ba kowa yasan da ita ba,sai mutane masu tarin muhimmanci cikin rayuwarsa kamar ita. Wasu irin warm gold lights......soft leather seats da qamshin oud mai laushi ke tashi,wani yanayi sak irin na mutanen da suka saba da rayuwar kudi da iko. Batasan me yasa bata gajiya da kallonsa ba.. ..d'an gayu ne gasken gaske,ita kanta ta shaida hakan. Har wani lokaci tana ganin kar yazo ya wucema gayunta,wani lokaci tana canza shiga ko kaya saboda ya dace da nasa class da gayun. Ta dauke idanunta a kansa, har yanzu jikinta na jin gajiyar duk abubuwan da suka faru a Agadez. Amma duk da haka,zuciyarta tana samun wani irin peace saboda mutumin dake gabanta. Yana zaune opposite d'inta. Laptop dinsa a bud'e. Yana amsa Messages da email dake da yawa kan wayarsa,wadanda bai samu daman dubasu ba. Wani lokaci kuma idanunsa suna kan laptop din nasa yana amsan business updates. Har a sararin samaniya rayuwarsa ci gaba take da tafiya. Amma duk da hakan......duk da wannan busy din na rayuwarsa duk bayan few minutes sai idanunsa sun dawo kanta. Always checking. Always aware of her. Wani murmushi ya qwace ma akhnan a hankali,data tuna yadda ya satota shigen abinda ya faru a wancan tafiyar tasu. “Ka ma manta ka yi wa Nanay sallama?.” ta fada da tsokana cikin muryarta tana son ganin reaction dinsa. Sai ya d'aga idanunsa daga screen d'in. Wani murmushi daya tsaya iya labbansa ya bayyana yana dubanta da narkakkun idanunsa. “I was in a hurry.” ya furta da nutsuwar nan tasa,muryarsa da wani irin laushi. Idanunta tayi rolling,wadannan blue eyes din da fitilar gurin ta qara musu wani irin kyau. “Hurry for what?” Sai ya rufe laptop din da wani irin slow,ya zuba mata ido da wani irin zurfaffan kallo. “To take you away from everyone.” Zuciyarta ta yi wani irin bugawa da wani irin laushi,ta sauke idanunta a nutse tana sakin murmushi. Ya ilaheee.....bazai dai qyaleta ba,duk da yadda ta zurma da yawa saiya sanya qilan zuciyarta bugawa saboda kalamansa da soyayyarshi. Ya miqa mata hannu. Ta sa nata cikin nasa. Kamar abinda yake jira kenan Immediately jawota zuwa seat din kusa dashi. “You’ve shared yourself with too many people these past days.” ya fadi da muryar rada kaman yadda ya saba mata magana yanzun. “Now I want you to myself.” ya furta maganan cikin kunnuwanta,daidai sanda jirgin yake ratsawa cikin duhun sararin samaniya,yayin da a cikin jirgin zuciyarta ke narkewa a hankali. *MAKKA* *_Raffles hotel_* Sun isa cikin dare. suka samu kuma qasaitaccen convoy na jiransu a wajen private terminal. Black SUVs masu tinted glass. Royal security. Kamar wancan karon.....haka akazo tarbarsa,abun wannan karon bai barta da mamaki me yawa ba,saboda ta gama sanin wayeshi. A yanzun dukkan mamakinta na sauqin kansa ne da rashin daukan kansa a bakin kowa. Idan taga yadda larabawan suke girmamashi suna gaidashi......ta tuna yadda yake treating nata da kulawa. Ya shiga kitchen ya hada mata abinci,ya tayata shiryawa sai taji wani tsoro ya kamata. Tsoron anya bata wuce gona da iri ba?. Ta jingina kanta a glass window tana kallon Madina. City lights masu haske da suka cika garin. Masallatai,kiran sallah daga masallatan dake nesa. Wani irin natsuwa ne a cikin garin,nutsuwar da babu inda zakaje ka riski kwantankwacinta sai a cikin garin me albarka. Haisam ya lura da yadda take kallon wajen. “Tired?” ya tambayeta da kulawa. A hankali ta girgiza kai. “No.” ta furta da wata nutsatsiyar murya. “I think my soul needed this place.” Sai ya kalleta na second biyu. Wani irin softness ya bayyana a idanunsa. Ya miqa hannunsa yana riqo nata a tausashe. “Mine too.” ya amsa yana kulle idanunsa tare da budesu lokaci guda. A hankali ta aza kanta saman kafadarsa. Tana jin a yanzu......lokaci yayi da dukkaninsu zasu samu cikakkiyar nutsuwar ruhi......tarayya me albarka da kuma qarin fahimtar juna a tsakaninsu. Wannan hotel din dai....wannan hotel din daya bar mata memories masu dadi cikin kanta. Memories din da bata taba zaton masu dadin bane sai yanzun da suka zama abu daya ita da haisam din. “Freshen up.” “We’re going for Umrah." Ya fad'a yana cire agogon dake daure a hannunsa. A kunyace ta fara rage kayan jikinta,saidai ta lura sam ma kamar hankalinsa baya kanta. Ya kammala cire komai yabar boxer a jikinsa. Ya dauki towel dinsa ya nufi bandaki kai tsaye,ita kuma ta dauke idanunta tana daure gashinta daya ware. Ta sakankance.....bata ankara ba ta jishi ya dawo,ya kuma dauketa cak yayi bathroom din da da ita ba tare daya tsaya neman ta bakinta ba. "Relax mana.....zamuyi koyi da sunnar manzon Allah....." Ya fada yana dakatawa daga bakin bathroom din,idanunsa cikin nata,fatarsa dake gogar tata sai taji kamar tana neman tada qura ne,abinda zai karanta mata hadisi ne,don haka bai yarda ya qarasa bakin bathroom din ba. "Nana aisha tace mun kasance muna wanka tare da annabi.....a cikin mazubin ruwa daya,sai ya kamfata nima haka,har hannuwanmu suna haduwa guri daya". "S A W" Ta fada tana motsa labbanta a hankali,tana jin kuma yadda qamshinsa ke fita direct daga fatar nan tasa data lullube gymnastic body dinsa. "Daga yau......inde ina guri......ba batun wanka daban daban......deal?" Ya fada yana fiddo mata manyan idanunsa. Kai ta gyada a hankali kunya tana narkata. "Deal" Ta amsa masa,sai ya saki murmushi ya kuma sanya kai zuwa bathroom din da ita. Shi ya taimaka mata ta shirya tsaf cikin baqar abaya data fidda sigar kyanta. Kaman yadda yakeyi a yanzun,shike taimaka mata da abubuwan daya lura bata saba dasu ba,suna bata wahala kuma tanaso ta koya din. Ya rage shigar birra sabgarsu,komai da takan kira birra shike mata,sai itama ta soma qoqarin yin abubuwan da kanta. Riqe da hannunta suka shiga haram. Fararen haske na bayyanar da wanzuwar ka’abah. Dubban mutane cikin ibada,ddu’o’i na tashi zuwa sama da neman amsawarsu daga ubangijin talikai. Akhnan ta tsaya lokacin da ta ga Ka’abah. Numfashinta ya dauke na wucin gadi,sai hawaye suka soma zuba saman kuncinta. Abubuwa da yawa take tunawa.....abubuwa da yawa suke dawo mata. Rayuwa gaba dayanta qarya ce da yaudara,wani irin muradadden alamari ne kawai a cikinta. Ta tuna mammina......da rayuwarta da ita a baya,wadda rai ko zuciya basu taba kawo faruwar wannna ba. Ta tuna mamminta,kowa dake zagaye da ita tana jin kamar yana da mahaifiya.....ita kadai ta rasa. Duk da a yanzun uwaye har biyu Allah ya ninka mata. Motsinta da komai nata yana kan idanunsa cikin kulawa da tattali. Kamo hannunta yayi da wani irin taushi da nutsuwa,sai ya matsa kusa da ita kadan. “Easy, habibti.” ya fada kukanta yana huda masa zuciya. Ta kalleshi da idanunta masu hawaye. “I can’t explain what I’m feeling…” ta fadi da rawar murya. Sai ya zuba mata ido. Then quietly “You don’t need to.” “I understand.” ya qarasa fada yana kulle idanunsa cikin nata. Abinda ya bata wannan qwarin gwiwar kenan. Abinda ya bata wannan energy din kenan.....abinda ya sanyata jin tana tare da wata GARKUWA a gefanta. Tare sukayi dawaf,cikin nutsuwa kuma a hankali. Cikin wannan kulawar da tattalin kamar wancan Karon. Ko kusa ko alama bai bada daman wani ya bangajeta ba. Ko kuss ko alama bai bawa wani daman ya tabata ba. Abinda ta lura kaman rijalil amn na bakin ka'aba sun rage adadin mutanen dake dawaf din sanda suka iso. Bai magana dasu ba.....da idanu ta fahimci suka gama komai,don haka cikin rashin cunkosu da janyewar jama'a taci gaba da dawaf dinta. A zagaye na qarshe ya riqeta....ya kaita gaban ka'aba,shi da ita suka kifa fuskokinsu. Idanunta a lumshe tana hawaye,zuciyarta a bude da tarin addu'o'i da fata.....kunnuwanta suka jiye mata sautinsa.....sautin addu'arsa da wani yanayi daya sanyata bude idanunta a hankali.💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 132* _________________________ *_SHUWA INCENSE AND MORE_* 😊 *_kai daga jin sunan basai an gaya maka ba_* *_kai daga jin sunan basai ka tambaya ko tsaya tunanin maganar me ake ba_* *_MAGANA CE TA GIDAN QAMSHI_* *BAFA GAMA GARIN QAMSHIN DA KIKA SABA JI BA HAJJAJU* *KINA QONA TURARE YANA QAURI* *KINA SAKA KHUMRA TANA BIN SHANUN SARKI* *WANNAN DIN TURARE NE DAKE DAWWAMA A DAKI DA JIKI.....DA SALON QAMSHIN DAKE MANTAR DA ZUCIYA DUK WANI B'ACIN RAI* *TASTED AND TRUSTED👌👌👌100% HAJJAJU* *NA DABANNE A CIKIN NA DABAN*🙌🏽🙌🏽 *idan akazo kan SHUWA INCENSE an tashi magana* *idan ma kinsan baki shirya jan magana ba a duniyar qamshi to kisha zamanki hajajju* *_zaku iya magana da ita kai tsaye ta wannan number wayar_* +234 704 229 3387 ___________________________ Da farko,addu’arsa cikin larabci ne.....tataccen larabcin nan dake sanyata jin mutuwar son yaren musamman a bakin haisam din. Sai kuma muryarsa ta sauya. Lower,deeper,kamar addu’ar na fitowa daga wani sirrintaccen muhalli na zuciyarsa. “Ya Allah…" Ya fada cikin qanqan da murya da qasqantar da kai. Ba yarima bane wannan......ba billionaire bane......tataccen bawan Allah me yawan tsoronsa takeji a yanzun tattare dashi. “Ka bani ikon zama alkhairi gareta......kasa na zama mafin alkhairin maza a gurinta.kamar yadda manzonka muhammad S A W ya zama ga nana khadeeja” “ya Allah.....kar ka sanya ni dalilin ciwon zuciyarta.” "Ya Allah......kada ka qaddaramin son wata macen.....ko kwadayin aurenta. Ka wadata idanuna da zuciyata da khadeeja muhammad hammud kadai......" "Ya Allah.....kada ka bani daman ganin komai da zai burgeni daga wata macen......ka tsaida amincina idanuna da zuciyata akan khadeeja muhammad hammud ita daya har abada" Bugun zuciyarta dama numfashinta dukka suka dakata na wucin gadi. Saboda bata taba jin Haisam yana magana da wannan softness din haka ba. Sake jin muryar nan tasa tayi wadda ta sakeyin can qasa sosai,da alama sirri yake da mahaliccinsa......amma sai taji ko yaya tanason jin wannan asirin zuciyar. “She came to me carrying wounds…” “…Ya rahman ya Allah ka bani ikon kula da zuciyarta yadda ya dace.” Hawaye ne suka soma taruwa a idanunta. Tana jinsa idanunta a lumshe,sai ya dan sauke numfashi,kamar yana qoqarin fadin wani abu mai nauyi. “idan ka qaddara 'ya'ya a tsakaninmu...…” “…make them loved before they are even born.” wannan karon dafe bakinta tayi da wani mamaki da farinciki. “Make our home soft for them.” “Make me gentle with them.” shuru ya sakeyi,kamar yana qoqarin controlling feelings na zuciyarsa. Ya Allah…” “She made my heart peaceful.” “So don’t let me ever become a test for hers.” runtse idanunta tayi wannan karon,saboda a rayuwarta.....bata taba jin wani mutum yana addu’ar soyayya a kanta haka ba. Yanayin taji ya mata nauyi,sai taji meta roqa?,kaman ma bata roqa komai ba. Ya sauke hannayensa a hankali ya juya,sai idanunsu suka hadu. Kallon kallo ya shiga tsakaninsu idanun kowannensu da tsantsar qaunar d'an uwansa.....qauna ta fisabilillahi. Na second daya,second biyu.....uku.....hudu....biyar.....babu wanda yayi magana. Al'ummar duniya gaba daya suna motsi ko ina kusa dasu,gabansu da bayansu,amma a tsakaninsu kamar komai ya tsaya,ba abinda suke gani sai junansu. Akhnan ta qarasa gare shi a hankali tana rufw tazarar tsakaninsu,Idanunta cike da hawaye. “You prayed for me like that?” ta tambaya da mamaki zalla kwance a fuskarta. Sai ya zuba mata ido. Kamar baya ganin abin mamaki a ciki. “Who else would I pray for like that?” Zuciyarta ta motsa,tana kuma jin yadda take narkewa a kansa,ta kamo hannunsa da hannaye biyu. “You scare me when you love me this much.” ta fada tana girgiza kai sosai da gaske,quruciyar nan na harbawa sosai a fuskarta. Siririn murmushi ne ya subuce masa. “Good.” “Because you’ve done worse to me.” idanu ta sake zuba masa.....ta rasa me zatayi,kawai saita rungumeshi tsam a jikinta tana sake masa kuka. "Allah ka qaunaceshi ninkin yadda ya qaunaceni" Ta fada a fili.....ta kuma ninka wannan addu'ar a zuciyarta. Lokacin sa’ayi ta gaji kadan. Sai ya tsaya yana kallonta da tarin kulawa. “Do you want to rest?” Ta girgiza kai. “No.” “I want to finish this with you.” Wani irin kallo ya mata. Kallo mai nauyin cike da yabawa qoqarinta. “Then stay beside me.” “Always.” ya rufe maganan da wani murmushi daya sanyata jin kamar duk duniya kawai an halicceta ne saboda ita dashi. (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) Da wani tarin nutsuwa suka kammala dukkanin ibadar umra dinsu. Wani irin kusanci,suka zauna daga farfajiyar masallacin daga gefe,kansa saman cinyoyinta,yana fallasa mata sirrikan zuciyarsa. Sake narkewa kawai takeyi,saboda yadda kalamansa ke aikewa da wani makami mara linzami zuwa cikin zuciyarta,ita kuma zuciyartata tana rarraba saqon ga kowanne sashe na jikinta. Tun tana zaune sosai sai da taji zaman ya gagareta. Ta sunkuya ta masa rumfa da fuskarta tana jin dumin numfashinsa da yadda yake sake luguiguita zuciyarta da kalamai da suka qara saukar mata da nutsuwa bayan nutsuwar data samu tun bayan kammala ibadarsu. Tun a sannan.....tun a gurin tasan daren na musamman ne. Don basu koma hotel din haka salin alin ba. Ya riqe hannunta suka wuce wani gurin siyayyan kayan ciye ciye. "Tayani tafiya kawai zakiyi" Ya fada mata da muryarsa data canza mata tun a farfajiyar masallacin,yana aike mata da wani narkakken kallo me tsuma zuciya. Tayashin tafiyar kuwa kawai takeyi,ya dinga zagayawa yana tura cart yana tsintar kayan ciye ciye yana jefawa a ciki. Mamaki ya kamata,komai ya saka hannu ya dauka favourite dinta ne. Komai da zai dauka irin abinda takeso ne. Kamar mutumin daya saba mata siyayya shekaru da dama.....kaman wanda suka dade suna tare. Imported juice din da take sha a dare indai ta sameshi. Wani biscuit da ta taba ci sau daya a gabansa watannin baya. Har wani chips da ita kanta ta manta tana sonshi. "Haisamm" Ta kirashi data kasa jure mamakinta. Bai dago ba,still scanning shelves. "Mhm" Ya amsa mata. “How do you know all this?” Sai ya dauki wani snack ya jefa a cart din casually,still bai juyo ya kalleta ba. "You talk a lot when you’re comfortable.” shuru tayi tanason tuna yaushe tayi magana me yawa haka a gabansa har ya haddace komai?. "So kana haddace duk abinda nace?” ta tambaya da kokwanto. Wannan karon.....ya dago idanunsa kanta. Siririn murmushin nan akan labbansa. “I remember everything about you.” Zuciyarta taji ta harba a hankali. Sai ya juya zuwa wani shelf din,ya dauko wata dark chocolate box “This one.” ya dakata “You eat it when you’re upset.” Akhnan ta tsaya cak,saboda gaskiya ne,kuma bata taba gaya masa ba directly,sai ya dan juya kansa sashen da take. “You bite the corner first.” “Then pretend you’re not angry anymore.” Ta rufe fuskarta da hannunta cikin kunya da mamakinsa sosai. “This is actually scary.” yayi wata 'yar dariya me sauti kadan. “No.” “It’s love.” ya fada da husky voice din nan nasa dake komawa can ciki. Samun kanta tayi da kasa daina kallonsa,saboda yanzu take realizing yana lura da ita fiye da yadda ta zata. Yana adana qananun abubuwanta a zuciya quietly. *zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 08187255862 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 08187255862 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 133* ____________________________ https://chat.whatsapp.com/BkfPzSEDhnsIwyCD8LNGkm?s=cl&p=a&mlu=0 *IDAN KINSAN BA ORDER DIN KAYA ZAKI DINGA SAKAWA BA* *IDAN KINSAN BA BUSINESS KIKE DA NIYYAN YI NA KAWO KAYA DAGA CHINA BA KARKI SHIGA* *_DON ALLAH KARKI BATAWA KANKI LOKACI_* *_Assalamu alaikum my loyal people_* *_Barkanmu da wannan lokaci,kuma barkanmu da warhaka_* *_akwai da dama cikin mata wadanda suke sha'awar yin order kaya daga CHINA zuwa NIGERIA,NIJER,CAMERON,CHAD da GHANA_* *_Amma rashin samun amintaccen company....ko hannun wanda zasu dinga siyan kaya ta hannunsu cikin aminci ya hanasu_* *_To a yau addu'ar da yawa daga cikinku ta amsu,don nayo muku tsarabar kamfanin da zakuyi siyayya ta hannunsu su kuma dora muku kayanku har qasarku cikin aminci ba tare da fargaba ko d'ar d'ar ba_* *_kunsan komai nawa TASTED AND TRUSTED ne,to wannan kamfanin idan akwai abinda yafi TASTED AND TRUSTED ma shine_* *_Baki da fargaba kota sisin kwabo,ni SAFIYYA HUGUMA na tabbatar da hakan_* *_Zaki iya kasancewa dasu group nasu,inda a nan zaki hadu da agent dinsu da CEO nasu gaba daya ta wannan link din,zaki samu bayanansu da komai da ya shafi mu'amala dasu_* *INA ME BAKU TABBACIN AMINCI DA INGANCI DA SAUQIN MU'AMALA DASU DA IZININ ALLAH,BAN TALLATA MUKU SU BA SAI DANA GWADA* *Allah ya dafa mana,yasa mana albarka a nemanmu,ya albarkaci halal dinmu ameen summa amee* _________________________ Sai ya tsaya gaban fridge section. Ya dauki bottled drink dinta favourite. “You’ll ask for this around midnight.” “So we’re buying it now.” ta yi dariya har yanzu zuciyarta cike da almara. “Ka shiryawa rayuwata fiye da yadda na zata" Ta fada tana lumshe idanunta,kanta yana fasuwa,tana jin duk duniya ba macen data kaita sa'a da dacen miji. Matsawa kusa da ita kadan yayi,hannunsa still akan cart. “That’s because I plan to keep you for a very long time.” kasa magana tayi wannan karon,sai ta jingina kadan da cart din tana kallonsa. “You really like taking care of me.” Sai ya tsaya ya zuba mata ido,irin kallon da kullum ya mata shi kamar ranar ya fara ganinta. “No.” “I need to.” Ta lumshe idanunta a taqaice sannan ta budesu. Yadda ya fadi maganar kamar kula da ita ba aiki bane,wani bangare ne na numfashinsa. Hannunsa ya dora a kafadarta kaman yaron daya dafa yaro sa'ansa,ya fara tafiya da ita. "Bayan mata.....aminiya nake nema.....zaki zamemin ita?" Ya fada da dukkan gaskiyarsa,da sautin nan irin na mutumin dake neman daukin kulawa. Amini takeso.....itama amini takeso bawai miji kawai ba. Wannan shine burinta,ta samu amini......amintaccen da zata iya raba komanta dashi. Daidanta da rashin daidai dinta. Kyakkyawanta da mummunanta......dama komai.....idan tace komai.....tana nufin komai din da bazata iya boye masa ba. "Aminin na jima dama ina nema.....kaga idan aminiya ta samu amini....." ".....sai aminci" Ya qarasa mata da siririyar dariyar dake nuna nishadi. ".... Kina buqatar qarin snacks...." ".....ba wannan bake buqata ba" Ta datsi numfashinsa. Ta fada ne ba tare data kawo komai a ranta ba....amma yadda taga yana jifanta da kallo ya sanya ta dago cewa ya sauya manufar maganarta,daya buda baki yayi maganan kuwa sai da taji idan har qasa zata iya tsagewa,ba abinda zai hana kunya ta sanyata shigewa ciki. "Zaki samu.....wannan abun da kike buqata zaki sameshi.......ki shirya bani baby a daren nan" Ya qarasa fadi yana sanya tafin hannunsa ya kare bakinsa daga daya side din,kaman yana tunanin iska zata kwashi maganan ta kaishi wani guri. Dauke kanta tayi wata dariya me cakude da kunya tana ratsata. Maganan ta kasa barin kanta,ta daga hannunta a hankali tana shafa plate tummy dinta,tana imagination.....wai gata dauke da cikin yarima haisam din,sai wani murmushin ya qwace mata. Ta saba ya sakata tunaninsa koda yana tare da ita....hakanan ko yaya ya matsa daga gareta.....sai tunaninsa ya nunku. Yasan sirrin tsayewa a zuciyar 'ya mace.....baya taba barin zuciya da kwanyarta ta huta daga gareshi. A qafa suna hira.....hannuwansu sarqafe da juna....iskar makka tana kadasu me cike da wani irin aminci suka zabi komawa gida. Haka kawai ta samu kanta da shiryawa haisam kanta da kanta,irin shirin da macen da tasan kanta kanyi don tarbar miji. D'aya daga cikin lectures na nanany suna dawo mata daya bayan daya. Satar amsa kala kala akan hanyoyin jan hankalin miji,koda bai shirya mu'amala dake ba ya kawo kansa. A yadda takejin kanta a yanzu ta shirya.....sama da shiryawa ma bawai shiri kawai ba. Mijinta take buqata da gaske.....kuma zata karya wannan tausayin da space din da yaketa bata. Ta riga ta warke......tana jin a yanzu kasancewa dashi kawai take buqata. Wannan yanayin.......wannan duniyar......wannan rayuwar...wannan ruhin..... Wannan cudanyar tsakanin faffadan qirjinsa daya zame mata gida kuma mafaka.....da wannan skin din da takejin kamar ba wata fata a duniya data kaita qamshi sulbi da laushi. Tana sane ta sauya daki......saboda yau tana jin tana da wani sirrin gyara daban. Ta fidda sabulunta na mg's skin care products (806 299 1549). whole package din ta taho da abinta,bata bar ko daya a gida ba. Daki daki tayi amfani da kowanne sannan ta shiga wanka da sabulun. Ta fito fatarta tana sulbi da sheqi. Ta shirya tsaf cikin wata rigar bacci. Bata da shara shara can,amma muddin zaka zubawa mutum idanu.....kana iya hangen komai nasa tarwai cikin qwayar idanunka. Jikinta ta mulke da lallausan qamshin alfarmar nan na turarukan shuwa incense and more(+234 704 229 3387). Tun daga gashinta......zuwa kusfa kusfa na jikinta,sannan tabi bayansu da body milk din shuwan daya soma bin fatarta sosai ya zame mata jiki. Ita kanta qamshin burgeta yakeyi,ta dinga shaqarsa sosai har cikin hunhunta tana jin wani irin yanayi me kwantar da zuciya. Tana jin zai wahala batayi tattaki nigeria ta ziyarci matar ba. Tanaso ta ganta da ido,....taga wanne irin baiwar iya hada turare haka take dashi itama. Idan ta yuwu ma zata iya sanyata cikin masu bada shawarar hada qamshi sabon sample na turare idan zasu fitar daga maison akhnan. A nutse take takowa tana komawa dakinsun na asali bayan ta kammala shiryawa. Daren ya yi shiru sosai a suite din nasu,bayan doguwar ranar ibada da tafiya,sai taji komai ya ya nutsu kamar komai din shima yana neman hutu da nutsuwa ne. Sanda take tura qofa....Soft lamp light kawai ke haskawa a dakin. Iskar dare na motsa curtain a hankali. (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) Bata ganshi a dakin ba,sai wannan tattausan qamshin nasa daya barwa dakin wani yanayi me dadi. Ta qarasa a hankali ta zauna bakin bed din. Zuciyarta na harbawa da tsoro da kuma shakka. Karon farko zatayi wani abu ga mijinta don janye hankalinsa zuwa gareta. Tsoro takeji.....fargaba take ko zata burgeshi?. Idanunta ta lumshe taja iska sosai cikin hunhunta wadda ta taimaka wajen bata qwarin gwiwa,saita sake a hankali,ta zame dankwalin kanta,ta soma ware dogon gashinta cikin nutsuwa. Yau ta yi wani haske sosai,kamar an cire mata wani nauyi daga zuciyarta,haka take jinta sakayau.....haka kuma takejin wani nishadi. Ta tuna zaman cin abincinsu dazu ita dashi bayan sun dawo daga siyayya,sai murmushi ya subuce mata. Murmushin shima yayi,yana private musallah a tsaye,dauke da alqur'ani yana addu'o'insa sanda ta shigo. Ya ganta.....ya jita,ta kuma so daukan hankalinsa,amma saboda haske bai wadaci dakin ba,bai haska masa ita yadda yakeso ba....da kuma qur'anin dake riqe a hannunsa sai ya kama kansa,saidai kuma ya kasa yiwa idanunsa shamaki daga kanta. Ya kammala addu'arsa a nutse,ya ajiye qur'anin a muhallinsa. Already ya gama kashe wayoyinsa. No business. No meetings. No politics. Tonight.....attention dinsa gaba daya yana kanta. Ya zare jubah din jikinsa a hankali,wanda sai a sannan taji motsinsa. Qirjinta ya sake bugawa,ta maze kamar bata jishi ba tana ci gaba da ware gashin nata. Sanda ya fara takowa inda take zaune hannunta sai ya fara rawa kad'an,ya qaraso kusa da ita da wani tarin nutsuwa,wani irin shauqi na fusgarsa. Tsaiwa yayi kaman wani gunki yana kallonta na wasu seconds ba tare da magana ba. Sai ya miqa hannunsa ya kunna makunni d'aya,take haske ya gauraye dakin. Ta bayyana tarwai a gabansa. Idanunta ta runtse,tana jin wani fargaba yana kamata. Mutuwar tsaye yayi kawai,yana qare mata kallo. Tun daga tafin qafarta har zuwa saman kanta inda take ci gabada ware gashinta,saida hannuwanta dake rawa sun fallasata. “You look peaceful.” "You look dangerous habibti......oya come" Ya kirata yana komawa baya saman sofa yadda zai samu ganinta sosai ya zauna abinsa. "Come.....please" Ya sake fadi yana bajewa sosai saman sofa din. Ba abinda idanunsa ke buqata yanzu sai ganin wannan Kyakkyawar surar......da kyakkyawar siffar cikin kyawawan kayan baccin jikinta. "Kije.....lada zaki samu.....ya cancanci komai" Wani sashe na zuciyarta ke rad'a mata. Miqewa tayi a hankali ta jefa gashinta baya. Da wani irin taku da a yau tana sane ta sake qawatashi da wani irin yanayi da ita kanta batasan ta iya ba ta soma takawa zuwa gareshi. "Ya salaaamm" Ya fadi yana miqewa zumbur kaman wanda aka cijeshi. Ya kasa jira ta qaraso,ya fara takawa sai suka hade a tsakiya,ya kamota sosai yana ajiyeta cikin jikinsa ya mata wata zazzafar runguma yana hade bakinsa da nata. Sai daya zare mata duk wani saitinta da nutsuwar kanta......jikinsa da nata dukkaninsu sukayi wani irin laushi,ya zare bakin nasa a hankali,numfashinsa na fita da sauri kamar wanda yayi tseren gudu. "You can’t just appear looking like that.” ya fada yana girgiza mata kai. "Kina haukatamin qwaqwalwa......ke me kyau ce.....giiftii......me kyau ce ke ko babu kwalliya" Ya fada yana dora yatsansa saman zara zaran eyelashes dinta zuciyarsa na bugawa da sauri da sauri. "Looking like what?” ta tambaya yana juya fararen idanunta dake dauke da blue din qwayar idanu. Kanshi ya girgiza,yana sakejin kwadayin kasancewarsu a guri guda da kusancin da yafi wannan zurfi. "Beautiful enough to distract me from breathing.” kanta ta langabar gefe,murmushi yana kubce mata. "You exaggerate too much.” tattausan murmushi me cike da kasala da tarin feeling ya subuce masa. "I actually think I’m underselling it.” ta sauke idanunta cikin kunya,ta motsa da nufin kubce masa,sai yayi hanzarin riqota,baiyi qasa a gwiwa ba ya sake marabtarta cikin jikinsa,sannan ya fara takawa da ita zuwa faffadan gadon dake killace da wasu lausasan shimfidu. "You don’t even know what you do to me.” kunya ta sake kamata,ta cusa fuskarta a qirjinsa tana jin hannuwansa suna yawo a bayan ta.....saman kanta.....cikin lallausan sumarta da mazaunanta. "And what do I do to you?” ta tambayeshi sanda yake sauketa saman gadon,ta bude idanunta tar a kansa tana kallon tarin fitinar dake ciki. "You make difficult days feel easy.” “You make silence feel warm.” sai ya sunkuyo yana mata rumfa da faffadan qirjinsa. " And somehow…” “…you walk into a room and suddenly nothing else matters.” muryarsa can qasa da wani irin nauyi da saqo me zurfin gaske. "You stare too much" Ta fada tana dora yatsanta saman lips dinsa....wadannan lips din dake tafiya da ita. Qarasa zamewa yayi samanta,ya aza mata dukka nauyinsa,ta yadda bazai dameta da yawa ba. Idanusa cikin nata da wani irin kusanci da suke musayar numfashi. *zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 08187255862 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 08187255862 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 134* ___________________________ *_Amintaccen gurin siyayya_* *_ingantattun kaya akan ingantaccen farashin da ba irinsa a kasuwa_* *_BONONZA DA PROMO akai akai_* *dukka sai a HUGUMA CLOSET* *Duniyar kayan yara,mata,maza,dukka* *shaddodi,atamfofi,laces,abayas,jakankuna,takalma,agogo,sarqoqi,English wears,night wears,under wears,da duk wani nau'in sutura babba da qarami* *_Karki yadda ayi babu ke.....leqa kiga yadda closet din HUGUMA kullum ke cike da kaya akan farashi me kama da KYAUTA_* *_YAN SARI....YAN REPOSTING.....DA SARAKAN ADO MASU SIYA DON KANSU....DUKKA INA MUKU MARABA_*🤝🤝🤝🤝 https://chat.whatsapp.com/FrqgC0YmUWP4FPmUzYuLJX ___________________________ "That sounds like your problem now.” tayi dariya da wani irin laushi,ta juyo da fuskarta sanda yake dagata. " Minti daya....zanzo yanzu nayi maganin......" Bata bashi dama ya qarasa ba,saiji yayi ta fusgoshi jikinta. Ta sanya hannuwanta duka biyun tana riqe fuskarsa a cikin su,irin yadda yake mata,kafin yace komai....kafin ya sake kowanne motsi ta manne bakinsu guri daya tana cusa harshenta cikin bakinsa da wani irin salo. Wani irin saqo ta soma aike masa.....saqon daya gigitashi ya kuma fiddashi daga duniyar da yake ciki zuwa wata duniya ta daban. Ita kanta batasan a inda ta samo wannan qarfin halin ba. Batasan inda ta samo qarfin halin iya sarrafa miji da zurfi har haka ba. Tuni ta kaishi qololuwa,ta ingixashi,ta kuma azashi a muhallin daya sanya ya qarasa susucewa gaba daya. Muhallin daya sanyashi manta waye shi,ya manta matsayin nan nasa......tarin mulki.....sarauta dama qasaitarsa gaba daya. Tasa ya manta wayeshi.....wannan malamin.....wannan billionaire din.....wannan qasaitaccen dan binciken sirri dake hana manyan qasurgumayen masu laifi sukuni. Amma koda ya karbi ragamar....koda ya fara aike mata da nasa saqonnin saita fahimci girman tazarar dake tsakaninsu.....saita Fahimci nisan da yayi mata a wannan fagen da yawan tazarar daya bata. Sai daya sanya ta manta komai da kowa nata.....sai data daina gane komai da kowa sai haisam dinta. Wannan haisam din da takejin dukka duniyarta ta rataya a wuyansa......ta rataya a tafin hannunsa.....ta rataya tsakanin qirjinsa da hannuwansa. Basu sararawa juna ba.....saida dukkaninsu suka cimma gaci. Shi da ita sai da sukakai wannan bigiren da dukka zuciyoyi da rayukan ma'aurata ke fatan kaiwa. A lokaci guda....kuma a tare,abinda ya haifar da harbawar wata matsananciyar soyayya a jiki zuciya da gangar jikkunansu gaba daya. Ta dauka shikenan......ta dauka komai ya qare,saidai kuma wani sabon shauqin ya sake tashi dab da sallar asuba tsakaninsu. Wata sabuwar rayuwa ce da yanzu ta farata,wani baqon lamari ne a gurinta,don haka sanda komai ya sake kammala sukayi wanka da sallar asuba,komawa tayi saman gado ta nade ta soma baccin gajiya. Da qyar ta tashi tayi sallar azahar,ya bude mata abincin da yasa aka kawo sukaci tare,kafin ya fita ya dawo bacci ya sake daukarta. Can cikin baccinta ta jishi a jikinta da wani irin yanayi daya tilastata watsakewa daga baccin. "Please.....guda daya" Ya fada yana kanainayeta cikin jikinsa yana wani narke mata kamar qaramin jinjiri. Narke masa tayi cikin tsoro tana narkar da wuya. Bata saba ba.....a karon farko ta bashi har sau biyu,ace yanzun wani dadin yake nema. "Haisamm mana.......bacci" Ta fada tana ture hannunsa. "Giiftii......please habibty" Ya fada yana kanainayeta ta yadda ba zata samu hanyar tsira ba. Ba yadda ta iya.....haka ya cikata da soyayya da dadin baki. Sanda suka fito a wanka ta shirya tana kumburo fuska da wadannan lips din nata da suka karbi kalolin kisses da a yau batasan adadinsu ba,sai tayi zaune saman sofa bed tana sake tura baki gaba. A iya haka kawai ta soma fahimtar inda maganganun nanay suka sanya gaba a zaman lecture din data mata a jimma. Tana zaune daga gefe,hannunta harde a qirjinta. Ya gani.....kuma ya sani....clearly fushi takeyi dashi. Tun dazun take qoqarin ignoring dinsa. Taqi yarda ko idanu su hada. Da gaske ta d'anji jiki.......har tana tunanin ta samu small bruises a gurin. Ya rufe wayarsa a nutse,ya soma takowa inda take zaune. Saman qafafunsa ya durqusa,sannan ya kama kunnuwansa biyu ya riqe,kaman yadda dalibin da yayi laifi wa malaminsa yakeyi a yayin da malamin yaso horashi. Sau daya ta kalleshi saita dauke idanunta tana maidashi wani sashen. Minti daya.....minti biyu.....minti uku,ta dauka zai tashi daga gurin,amma sai taga kaman a sannan ya fara zama ma. Sau uku tana juyawa tana satar kallonsa,saisu hada idanu,sai ita kuma tayi saurin kauda kanta. Sanda ya cika mintuna ashirin har cikin ranta taji ha zata iya ci gaba da ganinsa durqushe haka a gabanta ba. Wannan yarima haisam din da zai iya yaqar duk duniya?,amma gashi a daki durqushe a gabanta?. Kamar ta taba martabarsa haka ta dinga ji. "Ni ka tashi" Ta fada a narke tana tureshi kadan. "Ni bazan tashi ba.....har sai matata ta fahimceni" Ya qarasa maganan yana komawa ya zauna sosai a gabanta yana tanqwashe qafafu kaman me neman gafara. "Haisammm mana" Ta fadi tana kallon yadda wayarsa ke haske da numbers na mutane masu muhimmanci dake kiransa. Wani murmushi ya saki.....lallausan murmushi yana duban tsakiyar idanunta daya gama karantar komai. "Yarima haisam?.....business tycoon?......shugaba a national intelligence security service?" Ya fada dukka yana d'age girarsa. "Dukka wadannan basu da amfani a tattare dashi idan babu ke.....ke khadeejatu" Ya fada yana nunata da yatsarsa. "Zan iya tsayawa na yaqi duniya.....zan iya fuskantar kowanne namiji nayi fito na fito dashi.....amma kekam...." Ya fada yana sake dubanta sosai. ".....bani da wannan juriyar" Ya qarashe fadi muryarsa can qasan maqoshinsa. "Come" Ya fada a tausashe yana mata nuni da gabansa. A nutse ta sauko a hankali tana zama a gaban nasa,itama ta tanqwashe qafarta kamar yadda taga yayi. Hannunsa ya miqa ya riqo nata a tausashe yana duban idanunta. "You’re cute when you’re angry.” mele baki tayi irin na yaron dake shirin sakin kuka a gaban mahaifiyarsa. "I’m still upset.” ta fada da wata yarinta tana harbawa cikin idanunta. Yau lumshe idanunsa yana budesu a kanta. "Okay...." ".....then stay upset beside me" Ya fada yana runtse hannun nata sosai a cikin nasa. Murmushi ne yaso qwace mata,da kalan kallon da yake mata kawai ya sanya zuciyarta wani irin sanyi. "Giiftii.....ni maraya ne" Ya furta a nutse. Da sauri ta daga kanta tana kallonsa. "Yes.....maraya ne ni......matatace itace gata na" Ya fada da wani irin tausayi da narkewa. "Kiyi haquri da yadda nazo miki......ya kamata ace yana d'aya daga cikin abubuwan da kika sani abubuwan dana gaya miki tun kafin zuwan yanzu.....tuzuru ne ni" Kalmar ta sanya dariya qwace mata,amma sai ta cusa kanta tsakanin hannuwanta tana boyewa. "Na jima ina tsare idanuna da kunnuwana dama dukkan gabbaina.......duk da irin yanayin halittata....." ".....giftii" Ya kirata a tausashe. Idanu ta zuba masa itama a tausashe. Sai ya matse hannunta cikin nasa,da alama maganan yana da muhimmanci me tarin gaske. (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) "Ina da buqata sosai giiftii.....ina da buqata amma ta matata kawai.....zaki taimakamin......ki fahimceni a yadda nake?.....ki kuma tayani ci gaba da kare kaina?". Maganan ta mata nauyi da yawa,kuma tayi daidai da maganar nanay. Sai tayi qasa da kanta tana jin rashin dacewar nuna fushinta. Ya kamata ace ta fahimceshi daga kalaman mahaifiyarsa kad'ai.....bawai ta hukuntashi ba. "Kayi haquri" Ta fada muryarta ta cika da wani irin laushi. Murza tafin hannunta yayi cikin nasa. "No need giiftii.....no need ki bani haquri,ni yafi kamata nace kiyi haquri,don kin auri miji me nauyin buqata....but...." Ya fada yana hadiye yawu a hankali. "Indai zaki kasance a gefena.....komai zaizomin da sauqi....zan sabar dake.....zan koya miki yadda zaki......" "Noooo....don Allah" Ta fada tana noqe kanta kunya tana cikata kaman zata nutse. Murmushi ya sauke,wani murmushi me sauti. "......da gaske.....zan maidaki irina.....zan koya miki k......" Bata shirya ba.....sai ganinta tayi a gabansa. Ta sanya dukka hannuwanta tana toshe masa baki. Ya saki dariya yana riqe hannun nata gami da saukeshi daga bakinsa. Ya miqe da wani irin zafin nama ya dauketa cak yana maidata gadon.. "Ka bari don Allah" Take fada tana qyalqyala dariya,saboda yadda ya danneta yana gaya mata maganganun da takejin sunfi qarfin kunnuwanta dama shekarunta gaba daya. Kafin barinsu makka.....batasan adadin dawafi da addu'ar data yiwa aurensu ba. Wani lokaci ma haisam baisan ta tafi ba. Mamminta kuwa batasan sau nawa ta ambaceta ta nema mata rahamar Allah ba. Addu'ar data yiwa sultane kuwa ta dabance. Komai ta samu....take kuma samu game da alfanun nagartaccen miji sultane ne sila. Shine ya mata hanyar data mallaki wannan LU'U LU'U din me tsada kamar yadda take kiran haisam a can birnin zuciyarta kadai. Don yaqi yarda......yana mutuwar son tace HAISAM da wannan basarakiyar muryar tata. Da gaske ne abinda suka gaya mata shi da nanay. Yana da buqata akan d'iya mace. Ta gani ta kuma shaida hakan,saidai bai qyaleta ta jigata ba. Da dukkan qoqarin bata support yake komai,inda daga qarshe dole suka kira nanay. "Ka gama sace sacen matar taka?,wai nikam haisam.....tunda akhnan taka ce....waye ya baka labarin za'a dauketa ko a rabaku?" Murmushi yake cike da kunya,wayar tana handfree a gefansu. Sumarsa kawai yake shafawa wadda ta qara cika baqi da santsi,idanunsa akan akhnan dake zaune kamar ruwa ya cinyeta. Batasan abinda ake kira da haqiqanin AMINCI KAUNA da shaquwa irin na d'a da uwa ba......sai da taga yadda nanay ta dago bayanasa ba tare daya zurfafa magana ko ya sauka daga hanya ba. "Bamu guri" Kawai tace masa,sai ya zame hannunsa daga cikin nata yadan matsa gefe amma bai tashi ba. Yaja bakinsa yayi shuru,yadda nanay zata dauka ya tashin....baya gurin. Da idanu take masa alamu....alamun ka tashi gaba daya ko na gayawa nanay. Yana dariya qasa qasa ya miqe ya bar musu gurin,ya koma can bakin window view na ka'aba yayi zamansa a can. Ta godewa Allah da nanay ta buqaci haisam ya matsa a gurin. Itakam ko tsakaninta da morsa safiyya kunya da maganganu irin wadannan bata taba jinta ba. Saidai ta samu fa'ida da dabaru masu yawan gaske da suka sanyata ta sake sosai da nanay. "Idan kun iso jimma.....akwai gyaran da zan miki idan ma akwai ragowar irin wadannan damuwan,komai naki da nashi zai daidaita in sha Allah" Rasa me zatace mata tayi.....rasa da bakin da zata gode mata tayi. Lallai ba shakka.....UWA Allah ya bata ita,wata uwa ta daban bayan morsa safiyya. *_MADEENA_* Gari ne da dukkan musulmi ke shauqinsa.....wanzuwa cikinsa kadai kuma yake bawa zuciya da ruhi nutsuwa da salama me yawan gaske. Isarsu madeena din ta sake bude wani sabon shafi a rayuwarsu. Ibada bata rinjayi bawa zuciya da ruhi hutu ba. Kalar ziyarce ziyarce iri daban daban da suka banbanta da na waccan tafiyar tasu ta farko. A yanzun....bawai iya guraren da suke da alaqa da tarihin addini kawai suka je ba. Aah....harda guraren da aka tanada kawai saboda ma'aurata irin ita da haisam. Social farm.....suka wuce kana mirror,gurin da taji kamar kada ta fita a cikinsa. Ya mata....ya gama yi mata,sannan ya sanya wata nutsuwa me yawa a zuciyarta da tarin qaunar haisam. Shi kansa yaga hakan a fuskarta da yanayinta gaba daya. A daren kuma ya samu kyakkyawan tukuici daga gareta,wanda ya sanyashi ya dinga murmushi shi kadai yinin washegari gaba daya. Ya kuma tsaya cikin haram na madeena bayan sun fito daga raudha ita dashi,ya mata addu'o'i masu tarin yawa da suka saka hawaye zuba a idanunta. Ita kanta ta sani.....yadda mijinta yake na daban.....haka soyayyarsu take ta daban ita dashi. Kaman daban aka halicci soyayyarta a zuciyarsa......da tashi soyayyar a zuciyarta. Sati biyu sukayi a madeena din,suka hada komai nasu da wata irin nutsuwar zuciya data ruhi da suka samu. Rayuwarsu ta koma kan saiti da wata irin nutsuwa da tarin fahimtar juna. *zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 08187255862 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 08187255862 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 135* __________________________ https://chat.whatsapp.com/BkfPzSEDhnsIwyCD8LNGkm?s=cl&p=a&mlu=0 *IDAN KINSAN BA ORDER DIN KAYA ZAKI DINGA SAKAWA BA* *IDAN KINSAN BA BUSINESS KIKE DA NIYYAN YI NA KAWO KAYA DAGA CHINA BA KARKI SHIGA* *_DON ALLAH KARKI BATAWA KANKI LOKACI_* *_Assalamu alaikum my loyal people_* *_Barkanmu da wannan lokaci,kuma barkanmu da warhaka_* *_akwai da dama cikin mata wadanda suke sha'awar yin order kaya daga CHINA zuwa NIGERIA,NIJER,CAMERON,CHAD da GHANA_* *_Amma rashin samun amintaccen company....ko hannun wanda zasu dinga siyan kaya ta hannunsu cikin aminci ya hanasu_* *_To a yau addu'ar da yawa daga cikinku ta amsu,don nayo muku tsarabar kamfanin da zakuyi siyayya ta hannunsu su kuma dora muku kayanku har qasarku cikin aminci ba tare da fargaba ko d'ar d'ar ba_* *_kunsan komai nawa TASTED AND TRUSTED ne,to wannan kamfanin idan akwai abinda yafi TASTED AND TRUSTED ma shine_* *_Baki da fargaba kota sisin kwabo,ni SAFIYYA HUGUMA na tabbatar da hakan_* *_Zaki iya kasancewa dasu group nasu,inda a nan zaki hadu da agent dinsu da CEO nasu gaba daya ta wannan link din,zaki samu bayanansu da komai da ya shafi mu'amala dasu_* *INA ME BAKU TABBACIN AMINCI DA INGANCI DA SAUQIN MU'AMALA DASU DA IZININ ALLAH,BAN TALLATA MUKU SU BA SAI DANA GWADA* *Allah ya dafa mana,yasa mana albarka a nemanmu,ya albarkaci halal dinmu ameen summa amee* _____________________________ ★★★ *_UNITED STATE U SA_* *_AMANGIRI RESORT UTAH_* Batasan daga madeena ina suka nufa ba.....don bai gaya mata ba,saidai kawai ya ware mata wasu kaya da tayi wata shiga data rufe jikinta.....amma kuma ta dace sosai da zamani. Idanunta akan allon da rubuce rubucen dake fadi mata cewa,sun sauka ne a canyonlands regional Airport. Idanunta a kansa time to time kamar me tuhumarsa inda zai kaita,saidai kuma ya basar,yayi kamar bai gani ba da wannan attitude din nasa. "Ina zaka kaini ne?" Ta tambayeshi tana gaza jurewa. Sau daya ya kalleta,ya sauke mata murmushin nan nasa,sannan ya taka yana bude mata murfin baqar motar dake ta sheqi dake tsaye a gabansu. Shiga tayi a nutse,ya matsa yana tattare mata rigarta cikin girmamawa,sannan ya daga idanu yana dafe hannuwansa a saman motar. "Kin tsorata ne?" Ya tambaya da tsokana fal muryarsa. Kai ta girgixa a hankali. "Kai din amintacce ne....wani ami tacce da bani da irinsa" Murmushi ya qwace masa yana jin taushin maganarta har tsakiyar zuciyarsa. "Akwai wuraren da sai mutum ya gani kafin ya fahimta.” ".....wannan yana d'aya daga ciki" Ya furta cikin kulawar dake nunawa ta cikin idanunsa. "Na kawo ki wajen da duniya ba zata damemu ba.” ya sake amsa mata har yanzu idanunsu kulle cikin na juna,kamar aikin da ya ragema rayuwarsu kenan. Ta dan murmusa,duk da qoqarin da take yi na boye curiosity dinta amma sai da tace “To idan ban son wajen fa?” A karon farko sai ya yi dan guntun dariya. “Impossible.” “Confidence kenan?” “A’a.” ya fada yana girgiza kai,ya jingina da murfin motar ya zamana yana tsaye opposite nata yana kallonta kai tsaye. “Na riga na san me yake kwace miki hankali.” “Really?" Ta tamabaya da kwantaccen murmushi akan labbanta tana d'age masa dukka girarta. “Silence… beauty… da kuma wajen da babu mutane masu damunki.” Ta kasa musa maganarsa. Sai ya kara da “Kuma idan kika gani…” Ya d'an tsaya yana kallon reaction d'inta. “Zaki manta kin taba tambayata inda zamu.” kai take jinjinawa da wani yanayi me nutsuwa a tare da ita. "Allah yasa" Ta furta sanda yake zagayowa ta daya side din saboda isowar driver din. Hannunsa na cikin nata sanda motar ta fara motsawa. Ya zame masa kusan al'ada,muddin suna kusa da juna baya gajiya da riqe hannunta. Har kunya takeji saboda baya ganin kowa sai ita a irin wannan lokacin. Ta sanshi.....yana daga cikin halayyarsa dabi'ar ban mamaki,sai ta samu kanta da zumudin ganin gurin da yace mata zasuje din,kuma a USA,to wanne irin guri ne haka da batasan dashi ba?. A hankali taga sun dauki wata hanya.....wata hanya da sam batayi kama da hanyoyin da dan adam yake yawan zirga zirga ta gurin ba. Sannu a hankali sai gasu sun fara ratsawa sahara da hamada sosai,mamaki ya sanya kanta kullewa qwarai. Da motar ta shiga cikin doguwar hanyar hamadar garin utah....sai khnan ta fara jin wani irin shiru da bata taba ji ba.Ba hayaniyar gari. Ba mutane. Sai duwatsu masu girma da hasken faduwar rana da yake lullube komai da gold color. Mamakinta ya gaza boyuwa sanda ta fara hango wata ginanniyar duniya a gabansu. Cikin sahara?....cikin duwatsu?. Sai a hankali AMANGIRI RESORT ya fara bayyana daga cikin duwatsun hamadar… Akhnan batasan sanda ta mike ta zauna sosai ba akan seat dinta. “…Subhanallah.” Bata ma san lokacin da kalmar ta fita daga bakinta ba. Wajen bai yi kama da hotel ba. Ya yi kama da wani boyayyiyar masarauta ce da aka sassaka daga cikin duwatsun hamada. Concrete mai launin ruwan kasa. Glass walls masu nuna desert view,water reflections,fire pits,minimalist luxury mai tsada sosai. Komai a wajen idan ka kalla kasan ba qaramin guri bane....ba kuma gama garin guri bane da kowa da kowa ke iya zuwa ba. Haisam yana kallonta fiye da wajen,yana monitoring na reaction dinta sosai. Burinsa gurin ya burgeta kaman yadda yake burge kowa,burinsa gurin yayi mata,duk kuwa da cewa ya riga yaga alamun hakan a fuskarta. Akhnan ta fito daga motar a hankali tana kallon wajen kamar mafarki.....kamar almara,komai a wajen tana dubansa daya bayan daya. Bata taba ganin guri irin wannan ba. An qirqiri komai cikin duwatsu da sahara?. Wanne irin guri ne wannan?. “Haisam…” “Hmm?” “Mutane suna rayuwa a nan gaske?” Ya dan sunkuyar da kansa kusa da kunnenta. “Only a few can afford to.” ta yarda da maganansa dari bisa dari sanda suke shiga ciki,staff dinsu suna nan nan dasu cikin kulawa. Tsarinsu da yadda suke tafiyar da baqi kawai ya isa ya gaya maka lallai sun saba karbar manyan baqi,kuma manyan mutane a kowanne sashe na duniya. Ta tsaya cak tana kallon suit dinsu bayan an shigar musu da luggage dinsu,an kuma samar da sauran duka abinda haisam yace a kawo din,banda coffee da sukace yanzu zasu kawo,oromian coffee dinnan nasa. Duka suite din kamar private palace ne,kaman kowanne guri da zaiyi masauki a duniya. (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) floor to ceiling glass walls,private heated pool,outdoor fire lounge,desert-view,bathtub,giant king bed mai white linen,soft hidden lights,private spa section,dressing room da ya fi wasu apartments girma,duk sai daya ja hannunta a hankali da wani irin kulawa don ya tabbatar komai yayi mata yadda takeso. Amma abin da ya fi girgiza Akhnan…...shirun wajen. Kamar duniya ta tsaya musu cak,ba wanda kuma ya rage a cikin ta,daga ita saishi. Ta juya a hankali tana kallon Haisam. “Ka taba kawo wata mace nan?” ta masa tambayar tana jinjina yadda yasan kowanne guri daya dace da ma'aurata....ba'a iya qasarsa kawai ba....a qasashen duniya daban daban. Idonsa ya tsaya a kanta na wasu seconds. Kishi.....ya fada qasan ransa,dariya yakeso yayi,amma yasan idan yayin zai jawa kansa jagwal,shi da yake buqatar dare mafi tarihi a amangiri din.....ba iya wannan daren ba.....ya shirya musu yadda zasu lalace sosai shi da ita a gurin,sai kawai ya fuske “No.” “Da gaske?” ta sake tambaya. Ya lumshe idanunsa,sai a yanzu ya yarda da kalar rigimar mata. “Ban kawo kowa cikin duniyata haka ba.” ya fada yana cire agogonsa yana ajiye wa a hankali. Idanunta ta zuba masa tana jin tarin qaunarsa a ranta. Royal billionaire aura dinsa ya kara fitowa,calm,untouchable,dangerously composed. Ya taka zuwa glass wall din yana kallon desert sunset,yana sake girmama iko da buwayar ubangiji,yadda launin sama ke sauyawa a duka lokaci irin wannan. Sai ya juyo gare ta. “But you…”Ya tsaya kadan. “You belong here.” idanunta ta lumshe a hankali,tana jin yadda yake sake shigar da ita wata sabuwar duniyar da batasan da ita ba,wani sabon lainin soyayyarsa dake taso mata kaman zai hallakata. "Ko a map.....babu gurin nan.....ko map ya kasa tattara gurin nan a cikinsa......haka nakeso na mallaki nutsuwarki.....zuciyarki da dukka lokacinki a wannan sabuwar duniyar" Ya furta da sautinsa me zurfi....wannan husky voice din da idan yana mata magana takeji kamar ya tabbata yana hira da ita har abada. Knocking din da akayi ya katse musu komai,wannan shurun....da kallon da yakewa cute face dinta yana jin duniyarsa duka ta tattaru a wajen. Ta bude idanunta tana sake saukewa a kansa sanda yake dawowa ciki,hannunsa dauke da tray me azabar kyau,wani irin Royal tray da aka shirya asalin oromian coffee dinsa da baya rabo dashi a ko ina. "Kai" Ta fada da sauri tana dora hannunta saman hancinta sansa tururin coffee din ya isketa har inda take sanda ya ajiye tray din ya soma zubawa don ya fara dumama cikinsa. "What?" Ya dago kai yana tambayarta da lumsassun idanunsa. "Wanne irin coffee ne wannan?" "Me ya faru?" Ya tambayeta yana duban mug din daya cika da coffee din da tun kafin yakai gasha yawunsa ya fara tsinkewa saboda yadda ya dahu sosai. Kanta ta girgiza tana kallon mug din da yake shirin kaiwa bakinsa. "Wannan kamar ba coffee dinka bane" Kadan yayi sipping,sannna ya saukeshi idanunsa cikin nata. "Shine.....ba abinda ya rabasu dana jimma" Taku biyu ta matsa baya tana yamutse fuskarta. "Dadi kakeji?....dadi yake maka?" Yadan tsaya da mamakin ganin kamar hankalinta yadan tashi,sai kuma ya dage mata girarsa duka biyun alamun yes. Kai ta girgiza ta juya,ganin tana neman hanyar fita ya kirata a tausashe. "Hey.....giiftii" Ta waiwayo a hankali tana jin iskar dakin kamar ya sauya mata. Da girarsa da idanunsa ya tambayeta,saita tura baki gaba. "Ni tunda ka shigo dashi naji iskar dakin ta canza". Idanunsa ya zaro waje,yana mamaki don shikam baiji komai ba. Yayi shuru irin na wanda ke nazari. "Okay" Kawai yace da ita,sai ya fara tattare tray din kawai,ya dauka yana zuwa ya wuceta a tausashe yana fadin. "Stay in your room,coffee ne yazo ya sameki,shine zai fita ya baki guri" Ya fadi da kulawa sosai cikin muryarsa. *zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 08187255862 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 08187255862 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 136* ___________________________ *_Amintaccen gurin siyayya_* *_ingantattun kaya akan ingantaccen farashin da ba irinsa a kasuwa_* *_BONONZA DA PROMO akai akai_* *dukka sai a HUGUMA CLOSET* *Duniyar kayan yara,mata,maza,dukka* *shaddodi,atamfofi,laces,abayas,jakankuna,takalma,agogo,sarqoqi,English wears,night wears,under wears,da duk wani nau'in sutura babba da qarami* *_Karki yadda ayi babu ke.....leqa kiga yadda closet din HUGUMA kullum ke cike da kaya akan farashi me kama da KYAUTA_* *_YAN SARI....YAN REPOSTING.....DA SARAKAN ADO MASU SIYA DON KANSU....DUKKA INA MUKU MARABA_*🤝🤝🤝🤝 https://chat.whatsapp.com/FrqgC0YmUWP4FPmUzYuLJX ___________________________ Idanunta ta lumshe duka sanda ya kammala fita daga dakin da coffee din. "What a simple man" Ta fada a hankali muryarta qasan maqoshinta. Batasan me yasa yake da sauqin kai har haka ba,da fari idan ka kalleshi.....zaka dauka zaiyi taurin kai.....zaiyi wuyar sha'ani.....kuma bazaiyi dadin mu'amala ba. Amma kuma sai ka mu'amalanceshi......sai kasha tarin mamaki. Mu'amalarsa da ita ya sanyata ta sake komawa bitar tarihin ma'aiki da mu'amalarsa da iyalansa,sai a nan ta fahimci tsantsar aiki da ilimi ne yake aikinshi a gurin. Komai yana qoqari wajen ganin ya kwantanta yadda annabi ya koyar. Taushinsa.....rahamarsa da tausayawa iyali. Yadda yakan tsokani matansa a gurare......tayasu hidima dama yi musu hidimar gaba daya. Sai taji yana sake burgeta,sai taji yana sake shiga ranta,sai taji a duniya tafi kowacce diya mace dacewa da abokin rayuwa na gari. Taji wani tausayinsa kadan ya taba zuciyar ta,sarki ne shi a gaban duniya......wani abun girmamawa da cika umarninsa.....amma a gida.....a gabanta,yana maida kansa kamar bawa saboda taji dadi. Ta taka zuwa babban glass door din dake corner din dakin tana tsayawa. Batasan me yahau kanta ba,amma dai ita taji qamshin coffee din ya mata strong da yawa. Ta sauke idanunta zuwa ga hasken waje dake shigowa,wanda ke nuna yadda rana ke bankwana da duniya. Gurin ya mata ya mata ya mata,har batasan yadda zata misalta ba. Yasan ko ina.....ko ina me kyau.....kowanne guri da zai bawa mace mamaki ya tsaya a zuciyarta. Ta dora hannunta saman glass din tana sakin murmushi tana kallon Huge glass walls. Soft lights. Warm neutral colors masu daukan hankali dake gurin. Ta tuna sanda suke shigowa private villa din nasu. A cikin duwatsu take,a cikin duwatsu aka ginata. A nutse ya tura qofar dakin yana shigowa bayan ya kammala shanye coffee dinsa. Yayi tsaye daga bakin qofar yana qare mata kallo. Duk sanda zai kalleta.....wata tauraruwa yake gani,ba khadeeja ba.....ba akhnan ba....ba biftu ba.....ba giiftii dinsa ba. Ya sauke hannuwansa yana takowa cike da nutsuwa. Batasan ya shigo ba,sai duminsa taji a bayanta,ya jawota yana rungumeta ta baya,ya dora habarsa akan kafadarta yana tayata kallon villas din dake gine cikin duwatsun amangiri din ta glass din. "This place doesn’t look real…” ta furta a hankali kamar me rada. Sauke idanunsa yayi yana kallon yatsunta daya shimfidesu cikin tafin hannunsa. Ba gurin ke masa kyau ba. Itace take masa,ita take haska gurin cikin idanunsa. Baya mantawa,zuwansu na qarshe da 'yan shidansa.......baiji wannan nishadin ba....baiji burgewar gurin a idanunsa kamar yanzu ba. "It's....." "......But you look better.” ya fada yana sumbatar dogon wuyanta da wani irin laushi. Tsigar jikinta taji ta zuba,tadan motsa kadan tana murmushin kunya "You flirt too much these days.” sai ya manneta a jikinsa da kyau kamar zai narke a jikin nata su zama abu guda. "I’m making up for lost time......ke dince....." Sai ya kasa qarasawa,idanunsa suna lumshewa gami da bude kansu. Yana tuna darare masu yawa data dinga fiddashi daga saitinsa. ".....bansan me zance ba" Ya fada jikinsa na wani irin laushi. Ya karantar da ita karatuttuka masu nauyi a madeena,ta kuma dauka da kyau. Yadda take sarrafashi abun yana kwance masa kai,har sama da yadda ya dauka zata iya..... Harda sabbin darasissikan da bashi ya bata ba. Ta bude hannunta da kyau,ta karbeshi da kalan rayuwar da yakeso,ta sakar masa ragamar kanta da kanta,tana kuma tayashi sarrafa komai yadda zai qayatar dashi. Da yace mata baya buqatar komai daga gurinta sai SOYAYYA QAUNA KULAWA DA LOKACINTA. Ta dauki dukkan wannan abun daya fada da muhimmanci. Yace mata bayason ra wahalar da kanta gurin neman hanyar da zata mallakeshi......saboda a mallakensa yake indai a kanta ne. Ya gama mallakuwa already,tun ranar farko daya aza idanunsa a kanta. Tayi dariya ranan sosai. "Amma.....fada mukeyi fa haisamm......bakaso mu hadu ko a hanya.....baka kallona.....ka dauka banyi noticing bane?" Ya lumshe idanunsa kana ya budesu yana murmushi. "Na sani.....bazan kuma manta ba......ina kishin mazan daketa zuwa ganinki da sunan aure ne........ina tsoron mu dinga haduwa kina kallon cikin idanuna,saboda banaso ki gane komai a lokacin. Ina tsoron naci gaba da ji da ganin mazan dake zuwa gurinki,kada naje nayi loosing control dina saboda kishi......" Sai ya dakata. ".....akhnan" Ya kirata da yanayin daya tilasta mata maida hankali kansa. ".....ina da kishi......ina tsananin kishinki akhnan......billahi zan iya rasa raina a kan kishinki....." Sai ya tsaya yana maida numfashi,kamar wani abu me nauyi ya taba ransa. "Zan iya yarda nayi sharing ko na rasa komai nawa......amma bazan iya daukan hakan a kanki ba" "Taka ce ni......takace ni har abada......" Ta fada tana shigewa qirjinsa. (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) "Daga ranar da na fahimci kaine kayimin ALFARMA.....ba nice na maka ba....daga ranan na yarda kaine kalan mijin da zan rayu dashi har abada". Ya riqeta sosai a lokacin yana sakin murmushi. Ya tuna....,ta riqe kalmanne sanda morsa safiyya ke warware mata sauran abinda bata sani ba game da aurensu. "Har abada ke mai ALFARMA ce.....kuma har abada ke kikamin ALFARMA bani na miki ba" Ta motsa labbanta zatayi magana,ya dora yatsansa akan lips dinta yana kashe maganan. A yanzu da suke tsaye gaban glass din,sai ya saka hannu ya juyo da ita. Kallon kallo suka yiwa junansu,ya motsa lips dinsa a nutse. "Do you know how many nights I imagined this?” " No chaos " "No danger" "Just having you somewhere peaceful.” kasa magana tayi,sai hawaye da taji sun cika mata idanu. Wacce irin qauna yake mata haka?. Kanta kawai ta dora saman qirjinsa tana sauke numfashi " We survived a lot" Sai ya rungumeta cikin jikinsa tightly kamar har yanzu yana tsoron rasata. "Yes" "But I’d survive it all again if it leads me here with you.” yadan sassauta riqon da yayi mata ya bata lite kiss a goshinta. Sakin daya mata sai taji kaman an saki wani abu daga jikinta ta rage nauyi. Tadan tafi baya kadan tayi tangadi. Ya riqeta da sauri yana duban idanunta. "you okay?" Ya tambaya yana duban ta. Bata sani ba.....itama batasan me yasa taji wannan dan qaramin dizziness din ba. Batason yadda qaramin abu a kanta yake sanyashi damuwa haka,ko yaushe dan adam kan iya jin canji a jikinsa,bai kamata nata ya dameshi ba. Ta tsaya sosai akan qafafunta tana son nuna masa normal takeji. "I'm fine" "Akhnan" Ya kira sunanta har yanzu yana riqe da hannunta cikin nasa. Muryarsa low ce,calm,amma akwai warning a ciki,irin muryar mutumin da baya son a boye masa abu. Tadan kauda kanta tana jin damuwarta tana damunsa da yawa. "May be I'm just tired" Ta amsa masa. Idonsa ya tsaya a kanta na wasu seconds kafin ya kama tsintsiyar hannunta zuwa bakin gadon ya zaunar da ita. "Okay......ya kamata ki wanka ko qarfin jikinki zai dawo.....right?" Kai ta gyada a hankali,ya sake mata murmushi,ya juya yana takawa zuwa bathroom wanda tasan ruwan wanka zai hada mata. Kaman ko yaushe tare sukayi wankan,ya kuma tayata ta shirya. Bai fasa tayata ba har yanzu,duk da ta iya yanzu abubuwa da yawa da bata iya yiwa kanta a baya. Yace yanzun shine amininta.....shine abu mafi kusanci da ita. No more BB's dinta. Birra barratu bara'atu bushira. Sallan magariba sukayi,sannan suka wuce private dining dinsu da suke da option biyu. Daya a cikin suite din nasu,dayan kuma a waje,inda zai basu daman ganin desert din sosai da duwatsun dake gurin. A waje ya zabi suyi dinner din,gurin ya mata wani irin kyau,haske tako ina me daukan hankali,wata irin nutsuwa da zaka dauka daga kai sai wanda kukaje gurin kuke rayuwa,sai kuma masu muku hidiman da komai idan suka kawo suka tafi shikenan. Iskar da yanayin gurin suna mata dadi sosai. Yadda ta sake ma kawai ya gaya mata gurin na musamman ne. Ya barta ta saka kayan da takeso,very lite. Hakanan da kansa yace mata tabar gashinta haka,basai ya saka komai ba banda 'yar siririyar bandana. Ya matsa kusa da ita yana shaqar qamshin hair mist din muryarsa tana rarrabewa da yanayin da ita kadai ke fahimtar meke faruwa dashi. "Inaso na kalli gashinki.....iska tana kadashi....from left to right" Murmushi ya qwace mata. Wato kowanne namiji da irinsa.....kuma kowa da abinda yake burgeshi daban,abinda nanay ta gaya mata kenan rannan. Ba uwa kadai bace.....ba uwar miji kawai bace.....aah. Ita din malamarta ce.....ta zamantakewa da rayuwa gaba daya. Idan suka fara waya saidai haisam ya koma gefe,har yanzu kuma ya kasa gane dame dame ake fada akan doguwar wayar da akeyi tsakanin nanay da akhnan. Wani lokaci dariya yake bata bayan sun gama wayar,saboda sai yayi wani shuru kamar maraya yana narke mata ido. Akwai randa ya gaji da jira,ya rasa yadda zai calling attention akhnan towards him. Yana da wani irin kishi na gaske a kanta. Da gaske bayason ta raba lokacin ta da kowa saishi. Sai ya saki siririyar qara wai coffee ya zube masa a qafa. Da kanta nanay tace subhanallah cikin rudewa tace. *zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 08187255862 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 08187255862 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 137* ___________________________ *_Amintaccen gurin siyayya_* *_ingantattun kaya akan ingantaccen farashin da ba irinsa a kasuwa_* *_BONONZA DA PROMO akai akai_* *dukka sai a HUGUMA CLOSET* *Duniyar kayan yara,mata,maza,dukka* *shaddodi,atamfofi,laces,abayas,jakankuna,takalma,agogo,sarqoqi,English wears,night wears,under wears,da duk wani nau'in sutura babba da qarami* *_Karki yadda ayi babu ke.....leqa kiga yadda closet din HUGUMA kullum ke cike da kaya akan farashi me kama da KYAUTA_* *_YAN SARI....YAN REPOSTING.....DA SARAKAN ADO MASU SIYA DON KANSU....DUKKA INA MUKU MARABA_*🤝🤝🤝🤝 https://chat.whatsapp.com/FrqgC0YmUWP4FPmUzYuLJX __________________________ "Jeki duba shi.....Allah yasa ba serious bane" Ita tasan ba wani coffee,kawai sharrinsa ne. Mutumin da ruwan da yake wanka dashi har tururi yake?,sannan idan ya tashi shan coffee din har mamakin yadda bayajin zafinsa take.. Tayi hasashenta daidai kuwa,don tana zuwa ya cafketa ya matseta a jikinsa. "Haka kawai.....saiki dinga raba min lokutana" Bai ma bata daman fadin komai ba ya shiga yin abinda yafi ganewa,a nan yabar coffee din nasa ya huce ya gantale,qarshe sai masu shara da gyara musu gurinne suka zubda shi. Kwata kwata saita rasa d'an d'ano a bakinta. Yayi juyin duniya taci wani abun amma duk abinda ta saka a bakinta a gurin sau daya biyu sai taji bai mata ba. Ya dakata da cin nasa abincin,ya kafeta da idanun nan nasa. Ya dafa bayan hannunta da yatsunsa,duminsu ya ratsata. “You barely ate.” “Bana jin yunwa ne.”ta amsa masa. “Coffee upset your stomach.” Ba tambaya yayi ba,observation ne a muryarsa. Ta yi shiru,don bata da tabbacin amsar da zata bashi. Kusan kwana biyu saura su baro madeena taji komai baya burgeta. "Is okay" Ya fada yana ciro wayarsa. Kira yayi cikin harshen turanci na sakanni,sannan ya katse,sai taga yana rubutu. Batasan dame dame ya rubuta ba,taga dai ya aika ya sake ajiye wayar a gefansa,yaci gaba da cin abincin saidai still idanunsa suna kanta yana observing nata. Saqo ya shigo,ya dauki wayar ya duba,sai ya miqe a nutse yana ajiyeta,ya taka yana fita a gurin. Ta bishi da kallo,yau tana sake tantance tsahonsa. Giant ne sosai ta yadda duka duka kanta yake tsayawa cikin qirjinsa,yayi wani kyau abinsa yau cikin wata tshirt da wandon da iyakarsa qasan qaurinsa. Daga nesa ta hangoshi dauke da babban tray niqi niqi. Bata taba daina mamaki idan ta ganshi yana hidima da ita. Ya qaraso gabanta ya ajiye tray din,sannan a nutse ya fara bude komai da yake ciki. Bayan ya kammala budewar sai yaja ya tsaya yana dubanta. Itama duka abincin take bi da kallo. Ya kusa kala goma,na qasa daban daban. "Ki duba wanda zaki iya ci na zuba miki.....idan duka basuyi ba sai a sake zabo wasu guda goman your royal highness" Ya fada yana dora tafin hannunsa a qirjinsa gami da rusuna mata kaman yana gaban boss dinsa. Dariya ya bata sosai,ta aza hannunta abaki tana rufe dariyarta. Daya bayan daya ta soma gwadawa,saidai duk cikin goman abu daya ne ya mata. Iya hakanma ya masa dadi,ya tsareta har sai da taci,saidai tana kammalawa wata irin kasala ta rufeta,dole suka koma daki,ya tayata tayi shirin bacci. Tana shiryawar yana mata fadanci. Ta gane sarai me yake nufi,can qasan ranta take masa dariya,baisan itama a cikin yanayin take ba. Kwana biyun nan har tsoron kanta takeyi. Kada fa ya zamana ya horata sama da yadda zai iya riqeta?. Sai take ganin kamar ma taso ta fishi zaqewa da kwadayin harkar,amma ko daya ba zata bari ya gane hakan ba,wannan dalilin ya sanya koda ta gama shiryawa saita haye gadon abinta tana basarwa. Fita yayi,ba jimawa ya shigo hannunsa da mug. Black tea dinsa ne,bai nema coffee ba wannan karon don kada ya sake takura mata ko ya bata mode dinta. Idanunsa a kanta,ya qaraso a hankali saman bedside drawer ya zauna. Ta daga kanta a hankali tana ruban kyakkyawar fuskarsa. Magana zatayi.....amma tururin black tea din ya bugeta,ya qarasa can cikin cikinta ya hatsinashi. Wani yunquri tayi kaman me shirin yin amai,abinda ya sakashi miqewa da hanzari,har cup din yana shirin subucewa daga hannunsa,ya samu ya ajiyeshi saman bedside din yana haurowa saman gadon da sauri yana tambayarta. "Are you okay?" Shuru tayi,dafe da mararta da taji ta karta saboda yunqurin aman da tayi,tana jin wani abu daya dunqule mata yana sauka a hankali. (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) Zama yayi sosai,ya jata jikinsa yana bata comfort yadda zataji dadin zaman sosai. Har ya lura tayi relax,sannan cikin nutsuwa ya tambayeta. "Bakya jin dadi giiftii" Ya fada kai tsaye maganan nasa kaman tana bata tabbaci ne bawai tambaya bace. Bata musa ba,ta daga masa kai a hankali. Tsarin rayuwarsu da suka soma aza kansu akai shine. Ba boye boyen komai a tsakaninsu. "Since when?" Ya sake tambaya. Ta kalleshi idanunta suna rusunawa. "Ban san yaushe ba" Ta fada a narke. Shuru yayi yana ci gaba da kallonta,kamar yana qoqarin hada wani abu a kanta. "We’ll see a doctor when we get back.” ya bata tabbaci yana gyara mata zama sosai a jikinsa,ransa yana masa ba dadi. Ta yi kokarin murmushi kadan. “Doctor? Haisam,it’s not that serious fa." Bai amsa nan take ba,sai ya zare hular kanshi da yakan saka duk sanda zaiyi sallah,fara qal da ita ya ajiye gefe,idanunsa har yanzu a kanta. “You almost threw up because of coffee.....then black tea shima?" “Ban yi amai ba.” ta fada a shagwabe,don ita zancan zuwa asibitine sam sam bataso. Don qilan azo kan lamari na allura babbar abokiyar adawar tata kenan. “Almost.” ya fada sa accent dinnan nasa na yaren French dake narka mata zuciya. Ta ja blanket kadan tana kau da ido. “Maybe saboda flight ne fa.” “Maybe.” ya furta shima,saidai yadda ya fada din ya nuna bai yarda ba sam. Ya zameta a hankali yana sauka don qarasa shigo da abinda zasu buqata. Shiru ya sake ratsa suite din. Sai qarar desert wind daga can wajen glass walls. Akhnan ta lumshe ido na wasu seconds. Jikinta na jin wani irin nauyi da wani baqon yanayi. Sai ta ji gadon ya motsa. Ta sake bude ido,hisam ya zauna kusa da ita sosai,har tana jin dumin jikinsa. “Come here.” ya fada yana wara mata hannuwansa gaba daya,da alama isowarta kawai yake buqata. “Haisamm" Ta kira a shagwabe. “Akhnan.” shima ya kirata da muryarsa low sosai. Ta matsa kusa da shi a hankali,zancan zuwa asibiti ne bataso,shi takeso ya janye. Nan take ya janyota jikinsa a tausashe,hannunsa daya yana bayan kanta ya tallafeta sosai yana mata wani zuzzurfan kallo. Cikin mintuna qalilan wanna feelings din me nauyi ya fara tasiri da zagayawa a gangar jikinsu. Suka fara mantar da junansu komai,sai wannan soyayyar....wannan qaunar... Sai muhammad da khadeeja din kawai. Wani abu game da yadda yake handling dinta tonight ya bambanta da kowanne lokaci. Extra kulawa kamar tana da wani abu fragile da bai kamata ya karye ba a jikinta. Hakan sai yazo mata da wani sabon salo,wani sabon salo da ya sake tafiya da imaninta da tunaninta. Sai taji kaman ba haisam din ba....kamar an sake sauyashi gaba daya. Ya sake mamaye zuciyarta da tunaninta. Wani iri halitta ne da ba'a taba yin irinsa ba cikin rayuwarta,kullum cikin shayar da ita mamaki yake game da komai daya shafeta. Bai barta ba,sai daya tabbatar shi da ita dukka sun kashe wutar data taso musu. Yanayin ya masa dadi matuqa da gaske,don ya fahimci kamar yanayinta ya sake canzawa gaba daya itama,kamar wata daban aka sauya masa. Ya samu kansa da zuba mata idanu bayan sun fito daga wanka,ya hanata saka komai sai towel din jikinta,yace a haka yakeso ya ganta. *zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 08187255862 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 08187255862 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 138* _________________________ https://chat.whatsapp.com/BkfPzSEDhnsIwyCD8LNGkm?s=cl&p=a&mlu=0 *IDAN KINSAN BA ORDER DIN KAYA ZAKI DINGA SAKAWA BA* *IDAN KINSAN BA BUSINESS KIKE DA NIYYAN YI NA KAWO KAYA DAGA CHINA BA KARKI SHIGA* *_DON ALLAH KARKI BATAWA KANKI LOKACI_* *_Assalamu alaikum my loyal people_* *_Barkanmu da wannan lokaci,kuma barkanmu da warhaka_* *_akwai da dama cikin mata wadanda suke sha'awar yin order kaya daga CHINA zuwa NIGERIA,NIJER,CAMERON,CHAD da GHANA_* *_Amma rashin samun amintaccen company....ko hannun wanda zasu dinga siyan kaya ta hannunsu cikin aminci ya hanasu_* *_To a yau addu'ar da yawa daga cikinku ta amsu,don nayo muku tsarabar kamfanin da zakuyi siyayya ta hannunsu su kuma dora muku kayanku har qasarku cikin aminci ba tare da fargaba ko d'ar d'ar ba_* *_kunsan komai nawa TASTED AND TRUSTED ne,to wannan kamfanin idan akwai abinda yafi TASTED AND TRUSTED ma shine_* *_Baki da fargaba kota sisin kwabo,ni SAFIYYA HUGUMA na tabbatar da hakan_* *_Zaki iya kasancewa dasu group nasu,inda a nan zaki hadu da agent dinsu da CEO nasu gaba daya ta wannan link din,zaki samu bayanansu da komai da ya shafi mu'amala dasu_* *INA ME BAKU TABBACIN AMINCI DA INGANCI DA SAUQIN MU'AMALA DASU DA IZININ ALLAH,BAN TALLATA MUKU SU BA SAI DANA GWADA* *Allah ya dafa mana,yasa mana albarka a nemanmu,ya albarkaci halal dinmu ameen summa ameen* ____________________________ Ta dago ido tana kallonsa. “Why are you looking at me like that?” Ya dan shafa gefen kumatunta da thumb dinsa. “I’m thinking.” “Dangerous.” A hankali wani siririn murmushi ya bayyana a gefen bakinsa. “You’re funny when you’re sleepy.” Ta so ta bashi amsa… amma sai ta tsaya saboda wani abu da ta sake ji can qasan mararta. Numfashinta ya canza kadan,idanunsa suka sauka kanta. “What happened?” ya tambaya yana jawota cikin jikinsa. “Nothing.” “Akhnan.” Ta dafe cikinta lightly ba tare da ta sani ba,sai ta gane abin da tayin ta soma motsa yatsunta. A hankali idanunsa ya sauka kan hannunta. Daga hannun… zuwa fuskarta yabi da kallo. “Haisam…” ta kirashi tana sauke hannun ganin wani zuzzurfan kallo da yake mata,bai amsa ba amma yaci gaba da kallonta,kamar akwai tunanin da ya fado masa “When was your last period?” ya tambaya yana tsaida dubansa tsakanin idanuwanta. Tambayar tasa ta sauka a tsakaninsu kamar wani abu mai nauyi. Akhnan ta kafe shi da ido na wasu seconds bata iya magana ba. “Haisam….." “When?” ya sake tambaya yana jin kamar ya kurma ihun kabbara tun kafin yaji amsar da zata bashi. Muryarsa har yanzu calm ce. Amma akwai intensity a cikinta. Ta kau da kai a hankali. “I don’t remember exactly.” Ya cigaba da kallonta. Kamar ya riga ya fahimci cewa tana son ta tuna.....amma tana avoiding answer din. Kasa nutsuwa tayi......a hankali ta mike daga jikinsa,bai hanata tashi ba,yana kallonta ta isa side table inda wayarta take. Yatsunta suka bude calendar din cikin sauri kadan. Sai ta tsaya,numfashinta ya dauke na second guda. Haisam bai motsa ba. Bai tambayeta me ta gani ba,yana kallon fuskarta kawai. Ta sake duba dates din,gyara tsaiwarta ta sakeyi tana kallon calendar din wayarta kamar numbers din sun rikide mata. Yatsunta suka tsaya kan screen din. One month. Then another. Numfashinta ya dan canza. A hankali ta sake dawowa tayi counting. Daga Madina......daga tafiyoyinsu......daga lokacin da rayuwarta ta cakuda data haisam,sai wani abu ya fado mata. Tun bayan saninshi.....tun bayan daren farko da ya fara shiga rayuwarta gaba daya......ta daina ganin period dinta. Zata iya tunawa.......period dinta na qarshe ta yishi ne kafin ya cakuda rayuwarsa da tata. A ranar data gama......a ranar ta zama tashi.....a ranar ta amsa sunan mace cikakkiya. Zuciyarta ta bugu da karfi,bata taba mayar da hankali sosai ba sai a yanxun daya tambayeta,saboda rayuwarta tun daga lokacin ta juye da tarin abubuwa. tashin hankali......canjin rayuwa......tafiye tafiyensu da emotions. Yanayi na sabon aure. Haisam din kansa,komai yazo mata lokaci guda,har bata tsaya ta lura da kwanaki ba,sai yanzu. Yanzun da yake tambayarta. Yanzun da jikinta yake acting strange. Ta sake duba dates din......again.....again. Kamar zata samu wata answer dabam idan ta kara kallo. Da kanta ta gaji,a hankali ta zauna gefen bed din. “Haisam…” Muryarta ta canza. Shi kuma tun kafin ta karasa magana… ya fahimci akwai fargaba a tattare da ita. Ya karaso gare ta a hankali “What is it?” Ta dago idonta. A karo na farko akwai real panic a idanunta “I… I don’t think I remember the last time." Idonsa bai bar fuskarta ba. “When exactly?” ta girgiza kai a hankali “I don’t know.”Sai ta hadiye yawu,tana tsoro sosai. “Everything became messy after you."Ta dafe kanta kadan. “Na dauka saboda stress ne…travel… hormones…” ta fada muryarta na kara raguwa. “But now I can’t even tell when it stopped.” Wani irin shuru mai nauyi ya cika suite. Haisam ya tsaya yana kallonta “Look at me.” ya fada yanata qoqarin qunshe dariyar data kusa minti goma tanason murqusheshi. Ta dago ido kamar yadda ya buqata. “Are you scared?” Tambayar tasa ta karya wani abu a kirjinta,saboda kafin wannan second din....bata ma fahimci tana tsoro ba. “A little.” Idonsa ya rusuna kadan. “For what?” ta hadiye wani abu. Tasan ana mutuwa....mutuwa akeyi sosai idan an samu ciki,tana iya tuna staffs dinta mata kusan uku da dukka suka mutu gurin haihuwa,bayan haka batasan komai game ea daukan ciki da haihuwa ba. Sai kunyar yadda zata kalli duniya da wannan abun dake turowa gaba. Duk wanda ya kalla kenan sai yasan me tayi ita da haisam?. “…I don’t know.” kawai ta zabi ta amsa masa da hakan. Shuru ya sake shiga tsakaninsu. Sai ya kai hannu ya cire wayar daga hannunta ya ajiye a hankali. (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) “No more thinking tonight.” “Haisam” “If it’s nothing, we’ll know.” “And if it’s not nothing?” A karon farko tun farkon daren… wani abu mai laushi sosai ya bayyana a kallonsa. Sai ya matsa kusa da ita har tana jin saukar numfashinsa. “Then,” ya fada cikin kasa-kasa da murya. “I guess the desert just became our witness first.” Cikin jikinsa ya sanyata,ya rufesu iya qugu,ya bude wannan glass din ta yadda zasu samu daman ganin desert din sosai dama taurarin dake lullube da sararin samaniya. A nutse ya fara magana akan abubuwan dake gurin da Muryar nan tasa da tafiso. Taurarin wajen......yadda hamada ke yin shiru da dare.......yadda yake son wajen saboda babu hayaniya. Akhnan ta gane abin da yake yi,yana kokarin cireta daga wannan tsoron ne ba tare daya matsa mata ba,Just… quiet protection. Taji wannan amincin har cikin zuciyarta,sai ta jingina da kafadarsa a hankali. Haisam ya sumbaci saman kanta a tausashe,Idonsa kuwa suna kallon desert darkness. Wani farinciki yakeji a zuciyarsa. Haka kawai yakejin yaqinin cewa zai wahala idan qwallonsa bata shiga raga ba. Indai hakanne tabbas yana cikin mazaje dake da sa'a. Yanason 'ya'ya sosai....ba daya ko biyu ba,yara masu yawa,da khadeejansa kawai kuma yakeson ya tarasu. Amma idan Akhnan tana bukatar lokaci kafin ta iya kallon gaskiyar.....zai jira har sai wannan lokacin yayi. Tun daga ranar yake wani kaffa kaffa da ita,kaffa kaffan da batasan dalili ba. Ya qara ninka yawan kulawarsa a kanta,Komai bayaso tayi. Ko fita sukayi tattaki cikin saharar....tafiya kadan take gajiya,sai ya zamana yana lissafe da sanda take gajiya din. Da sunkai wannan gejin zai tsaya ta huta. Abinda kawai ta yarda dashi bata da lafiya,normal rashin lafiya. Inda zaka tambayeta kawai zatace rashin kuzari ne yake damunta. Sannan kuma tana yawan gajiya,uwa uba yanzun ba Komai takeso ba.... Ta zama me zabe zaben abinci,da launikan qamshi daban daban. Amma wannan qamshin nasa.....har yanzu ba abinda ya girgizashi a zuciyarta. Yaso ma suyi using the sam perfume,amma ta girgiza kai tana lumshe idanunta. "A jikinka kadai nake buqatar jinsa......zanci gaba da jinsa a gurinka kai kadai" Ya saki lallausan murmushi yana yin qasa da idanunsa. ★★★Kwanakinsu a amangiri resort wasu irin kwanaki ne da bazasu taba gogewa daga memories dinta ba. Bata taba ganin guri me tarin nutsuwa a duniya irin gurin ba. Zaka rantse da Allah ku kadai kuke rayuwa,don duk kwanakinsu a gurin sau biyu kawai ta taba ganin wasu couples. Kowa rayuwarsa yakeyi cikin suit dinsa. *MORNING POOL* Waya dasu rumaisa ne ya kaita gurin a safiyar.....mutanen da kulli yaumin saisun kirata sun tambayeta yaushe zata dawo jimma,don already sun baro agadez. Agadez din data musu dadi kaman ba zasu koma gida ba,saidai kuma an qulla babbar alaqa tsakanin sarki ahmad da rumaisa. Don tana kyautata zaton abune da bazai dauki dogon lokaci bama. Hakanan Aanani,sun dinke da muhammad. Da farko dabara ya mata akan ta zama malamarsa,yana zuwa daukan karatu,sannu a hankali sai taga karatun da yake zuwa dauka nasa ya zarta nata,ashe zuwa karatun nasa akwai manufa. Ba ya wannan abun ya tsaya ba......Aisa da shehnaz........duka rumaisa ta fara qyasa mata. Khadeem dama da tuni ya nuna ra'ayinsa akan aisa. An riga an gama magana. Hakanan shehnaz,wadda dama anata kai ruwa rana tsakanin mahaifansa. Mamarsa shehnaz takeso,babansa kuma ya zaba mata wata,daga qarshe sultane ya yanke ya haqura gaba daya kawai zaifi kwanciyar hankali. Ana yin hakan mutallab ya sako kai..... Ba sabo ko shaquwa tsakaninsu.......amma kunya da nauyin haisam ya sanya ta bashi dama. Sai a sannan ta gane ashe sakiyar da ba ruwa takeso ta yiwa kanta. Sunata mata nuqu nuqu,ita kuma tace ba zatace komai ba sai sun fito sun gaya mata da kansu. Sannan zata wankesu tass ta rama tsiyar da suka mata,duk da tuni taji zancan har a bakin haisam. Kar tasan kar ne,sunsan halinta,saita rama duk wata tsiya da suka tabayi mata. A nutse take takawa a gurin,desert sunlight na shiga glass walls da infinity privaate pool din villa din nasu dake gabanta suna haske mata idanu. Koda ta gama wayan zama tayi a nan,a bakin ruwan tana shaqar daddadar iskar saharar dake tuna mata da agadez. Ta baro haisam a ciki yana amsa waya shima. Ta danyi nisa kadan cikin tunanin rayuwa. A hankali taga inuwarsa tsaye a bayanta daga poolside. Takowa yayi yana dawowa ta gefanta,inda zaifi ganinta sosai. Ya zube lumsassun idanunsa da kullum ta kallesu abu daya suke gaya mata. "Ina buqatarki.....na har abada a cikin rayuwata" Yana sanye da baqin trouser da tshirt me laushi me gajeran hannu,itama baqa. Ta zauna masa sosai a jiki da wani kwantaccen kyau. Tunda sukazo gurin bashi da wata sutura sai irin wadannan kayan. Three quarter short ko long trouser da sauransu. Kallonta yake tana sake kwanciya saman ransa. A kwaakin wani glowing take qara yi,abinda ke qarfafa zarginsa a kanta kenan. Duk da har yanzu taqi bada hankalinta da gangan bare ta fahimci abinda ke gabanta. Zai qyaleta,har sai sanda komai ya mata ba zata. Dariya me laushi takan qwace masa a duk sanda ya hango ranar.....ranar da zatayi realising tana dauke da baby. Yana iya nasa qoqarin gurin bata kulawa da kariyar daya dace ace ta samu. “You keep staring.” ta fada tana tura baki gaba kadan. *zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 08187255862 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 08187255862 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 139* __________________________ *_Amintaccen gurin siyayya_* *_ingantattun kaya akan ingantaccen farashin da ba irinsa a kasuwa_* *_BONONZA DA PROMO akai akai_* *dukka sai a HUGUMA CLOSET* *Duniyar kayan yara,mata,maza,dukka* *shaddodi,atamfofi,laces,abayas,jakankuna,takalma,agogo,sarqoqi,English wears,night wears,under wears,da duk wani nau'in sutura babba da qarami* *_Karki yadda ayi babu ke.....leqa kiga yadda closet din HUGUMA kullum ke cike da kaya akan farashi me kama da KYAUTA_* *_YAN SARI....YAN REPOSTING.....DA SARAKAN ADO MASU SIYA DON KANSU....DUKKA INA MUKU MARABA_*🤝🤝🤝🤝 https://chat.whatsapp.com/FrqgC0YmUWP4FPmUzYuLJX __________________________ “You keep giving me reasons to." Ya amsa mata calmly yana sunkuyowa kanta kadan. Hannu ta saka a cikin ruwan wanda ta tsoma qafafunta a ciki,ta debo kadan a hannunta ta dan watsa masa. Sai ya tsaya still,then slowly ya cire agogon hannunsa. Akhnan ta zaro ido da sauri “Haisamm" Da wannan muryatata da kullum zata kirashin kashe masa jiki takeyi. Saidai it's too late daga sanda ta kirashin,don tuni ya shiga pool din straight toward her. Calm.....focused.....dangerously.....attractive Ta soma ja da baya tana dariya da wannan sautin nata dake shagaltar dashi. “No.....don’t start.” ta fada tana qoqarin zame qafafunta don ta samu ta gudu. “You started it.” ya fada da low voice dinnan nashi me zurfi. Ya samu nasarar kamo hannunta gently,ya kuma jawota cikin ruwan,sannan ya sake matso da ita cikin jikinsa. Close enough da zataji numfashinsa. “You’re happy here.” ya fada yana kallon blue eyes dinta daya cika da tsoro,da digo digon ruwa daya barbazu saman fatarta me santsi da sheqi,wadda sabulun Mg's skin product ya sake karbarta sosai.(806 299 1549). Ta kalleshi da wani zuzzurfan kallo sannan ta gyada kanta. “I’m happy anywhere…” “…you let me rest.”. Wani irin softness ya bayyana a idanunsa,sai ya dora goshinsa a nata. “Then rest with me forever.” Kai tsaye bedroom suka koma bayan gama wankan,saidai suna shiga wayarsa nata ruri tana maimaitawa,sai ya taka zuwa gaban madubi ya dauki wayar. "Omar" Ya furta a fili yana zama saman sofa ya daga kiran ya sakata a hands free gami da yin cikakkiyar sallamar nan tasa. “Omar.” ya kira ssunansa Shiru,sai muryar Omar ta fito qasa qasa da wani canji a cikin ta “Haisam…”ya kirashi da wani yanayi,nan take idanun Haisam suka dan sauya. Dukkaninsu suna iya gane yanayin junansu su shidan daga muryar 'yan uwansu. “What happened?” daga daya bangaren......numfashin Omar ya fito a hankali kafin ya amsa. “Mammina ta mutu.” maganan ya maqale cikin iska yana yawo. Akhnan da ke gefen gadon ta d'aga kanta kamar me ciwon wuya. Haisam bai motsa ba. Ko qyafta idanunsa baiyu ba na wasu seconds. “Sun same ta a daki ta rataye kanta.” “Ta bar letter.” omar ya sake fada "Ta rubutata da manja na abincinta da tsinke." Wani irin shiru ya cika suite din har Akhnan ta fara jin zuciyarta na bugawa. A hankali Haisam ya juya baya ga glass wall din. “Omar.” kafin yace komai omar yaci gaba da bayani. “She didn’t wait for trial.” “Ta ce bazata jure humiliation ba,ba zata juri qasqanci a idanun maqiya ba" Haisam ya rufe idonsa na second guda. Ba wai saboda shock kadai ba......sai saboda ya san Mammina......ya san pride dinta. Ya san yadda take kallon duniya. Baya ga haka.....girman nauyin data daukawa kanta,bata tsaya an sauke mata shi ba tun a duniya.....bata tsaya an rage mata nauyinsa ba.....ta sake daukar wani gangamemen nauyin,nauyinma cikin haqqin Allah me gaba daya. Har yanzu haisam ya gaza cewa komai,tsigar jikinsa kawai ke tashi. Ba don komai ba.....sai don hasaso nauye nauye daki daki dake rataye a wuyan mammina. An yankewa tamim dama dukkan wanda aka kama da laifin kisa hukuncin kisa. Masu cin amanar qasa kuma an musu nasu hukuncin daidai dasu. An saki yalwa bayan an horata,an kuma koreta kwata kwata daga masarautar agadez ba ita ba rayuwa a cikin ta har abada. Omar ya sake magana cikin gajiya. “The letter is mostly for you.” A hankali yatsun Haisam suka matse kan wayar,ya sani....zata rina....zata aikata. Ya sani duk duniya haushinta a kansa ne,koda ta mutu salin alin....zuciyarta zata tafi lahira ne da burin daukan fansa a kansa. (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) Akhnan ta mike tsaye ta kasa zama jin zancan letter da kuma sunan haisam. Tana kallonsa. Something about his face changed. Ba tsoro ba.......ba tashin hankali ba. Sai wani heavy stillness. “I’ll call you back.”Ya kashe wayar a hankali,sai ya rubuta masa gajeran saqo akan yayi scanning paper din ya aiko masa da saqon. A yanzu bayason duk abinda akhnan zataji da zai sanya ko yaya ta kwana ba cikin farinciki ba. Ya gaji hakanan,bayaso taji komai idan ba alkhairi ba. Sunan mammina da case dinta wani abune daya kamata ace an rufe babinsa har abada. Zai roqa mata rahama da sassauci gurin Allah,amma baya ga haka,baida wani power akan lamarinta,wannan tsakaninta da ubangijinta ne. “Haisam…” Bai amsa ba nan take. Sai ya ajiye wayar a hankali kan table. Ta matso kusa da shi,a hankali ta kamo hannunsa cikin nata. Ba wai saboda ta san abin da zata ce ba. Sai saboda suddenly… bata son ya tsaya shi kadai cikin wannan silence din. "Shikenan.” ta furta tana lumshe ido kad'an “Komai ya wuce…” sanda ya rigata sake magana muryarsa ta yi qasa sosai. “Komai ya qare.” ta sake fadi itama. Kalmar ta tsaya a tsakaninsu cikin nauyi....ba wai yana magana akan Mammina kadai ba. Yana magana akan rikice-rikicen da suka bi su a bayan rayuwarsu. Akhnan ta kalleshi cikin nutsuwa,sai ta ga abin da bai taba furtawa ba. Ya gaji.....ba da komai ba,sai da abinda dukka ya shafi mammina. A hankali ta matso kusa da shi. “Haisam…” kama fuskarta yayi cikin tafukan hannayensa ya sauke goshinsa a kanta na second guda. Sai ya rufe idonsa yana furta “I just want peace now.” Wani irin tausayi mai nauyi ya cika zuciyar Akhnan. Saboda ta gane,mutumin da duniya ke gani a matsayin untouchable… a wannan daren, yana neman gida ne kawai. Wannan gidan kuwa itace.....jikinta ne......kulawarta ce,batayi qasa a gwiwa ba ta soma bashi wannan gidan,tana mantar dashi komai da zafafan 'yan aike. Sai daya tabbatar da baccinta yayi nisa sannan ya miqe ya koma ga wayarsa,yana budewa hoton wasiqar yana fadowa email dinsa. Ya zauna a hankali ta yadda motsinsa bazai tasheta ba ya soma karantawa. Haisam Na tsane ka. Wataqila wannan shine abu na qarshe da zaka taba ji daga gareni,amma bana son tafiya ba tare da ka san cewa kai ne mutum na farko da ya sa na ji tsoron kaina. Ka rushe komai. Ba saboda ka qi sona ba…ko na kasa samun goyon bayanka ba, sai saboda ka kalli raina da burikana kamar basu da wani muhimmanci. A rayuwata ban saba da rashin samun abin da nake so ba. Amma a kanka!. Ka bani abu mafi muni fiye da wofantarwa da rashin nasara,wannan shine. Wulakanci. Ka sanya mutane suna kallona da tausayi. Ka tozarta alfarmata,ka kashe mafarkin dana shekara sama da arba'in ina ginawa tun quruciyata. Ni. Mammina. Ban iya rayuwa cikin wannan ba. Ban juri qasqanci ko rayuwa qasan kowa ba Daukaka na sani,jagoranci ne dabi'ata. Tunda dukka na rasasu....na fi son na bace da in tsaya ina jiran a yanke min hukunci kamar wata mara daraja. Ka ci nasara, Haisam. Ka kare matarka. Ka kare sunanka. Ka kare duniyarka. Ka kare ahalin matarka.....tabbas na sara maka da wannan namijin qoqarin.....na yaba maka,na kuma taya akhnan murnar samun namijin duniya irinka Amma kada ka taba tunanin baka lalata tawa rayuwar ba....kaine ka lalatata,kaine silar mutuwata. Zan tafi barzahu qiyayyarka a raina.....data akhnan da dukkanin jinin safeena Mammina. "Subhanallah" Ya maimaita har sau uku yana lumshe idanunsa. A hankali ya motsa labbansa. "Ba shakka abinda Allah ya fada a qur'ani gaskiya ne. Wanda Allah ya shiryar shine shiryayye.....duk wanda kuma Allah ya batar ba wanda zai shiryar dashi. Yaga wannan ayar a zahiri kan mammina,sai ya shiga ya goge saqon gaba daya,don baida wani amfani a gurinsa. *zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 08187255862 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 08187255862 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 140* ________________________ *_Amintaccen gurin siyayya_* *_ingantattun kaya akan ingantaccen farashin da ba irinsa a kasuwa_* *_BONONZA DA PROMO akai akai_* *dukka sai a HUGUMA CLOSET* *Duniyar kayan yara,mata,maza,dukka* *shaddodi,atamfofi,laces,abayas,jakankuna,takalma,agogo,sarqoqi,English wears,night wears,under wears,da duk wani nau'in sutura babba da qarami* *_Karki yadda ayi babu ke.....leqa kiga yadda closet din HUGUMA kullum ke cike da kaya akan farashi me kama da KYAUTA_* *_YAN SARI....YAN REPOSTING.....DA SARAKAN ADO MASU SIYA DON KANSU....DUKKA INA MUKU MARABA_*🤝🤝🤝🤝 https://chat.whatsapp.com/FrqgC0YmUWP4FPmUzYuLJX ________________________ A kwanakin da suka yi a Amangiri, Akhnan ta fara fahimtar wani bangare na Haisam da duniya bazata taba gani ba. Sai ita kadai,sai ita daya ita khadeeja muhammad hammud. Hamadar wajen ta kasance da wata irin cikin nutsuwa da kuma wani irin yanayi me kwantar da hankali… a karon farko a rayuwarta,shiru bai tsoratar da ita ba. A karon farko ta fahimci ma'anar shiru.... A karon farko ta gane shiru wani abu ne dake bada alamu na nutsuwa cikakkiya tare da shi. Ta kalli yadda yake lura da qananan abubuwa game da ita ba tare da tayi magana ba. Yadda yake rage muryarsa idan zai mata magana. Yadda yake cire duk wani abu da zai dame ta kafin ma ta furta,tare da cika mata komai da take so take muradi kafin ma takai ga furtawa. Kuma duk da ikon da yake da shi… a wajen, bai yi kama da mutumin da duniya ke tsoro ba,sai wani mutum da duniya take girmamawa matuqar girmamawa. A idanunsa take ganin mutum mai gajiya da yake neman wajen hutawa a tare da matar da yake so. A wasu dararen,Akhnan kan tsaya tana kallon desert lights tana tunanin yadda rayuwarta ta sauya. Cikin lokaci kadan daya wuce ta taba jin tsoron duniyar haisam. Tsoron irin ikonsa.....tsoron izzarsa da irin girman da yake da shi a idanun duniya.....daga qarshe ta soma tsoron soyayyar da zata iya cinye mutum gaba daya,saboda girmanta da fadinta. Amma a Amangiri… ta fara jin wani abu daban. SAFETY. Ba saboda wajen ba,sai saboda shi. Ya bata wani irin aminci cikin rayuwarta. Ya bata tabbaci.......sannan kuma ya bata yaqini na har abada. Ko lokacin da jikinta ya fara canzawa, canzawar da ta sani da gaske ne yana sauyawar. Lokacin da tsoro ya fara shiga zuciyarta,haisam bai matsa mata ba. Bai tambayi abin da bata shirya furtawa ba. Bai tilasta mata fuskantar gaskiyar da take gudu daga gare ta ba. Sai dai ya tsaya kusa da ita cikin nutsuwa… kamar yana gaya mata cewa ko menene zai zo, bazata dauke shi ita kadai ba. Kuma a cikin shirun hamadar da babu kowa sai su biyu…Akhnan ta fara gane cewa wata soyayyar bata zuwa da hayaniya. Wata soyayyar tana zuwa ne da kulawa da nutsuwa, hannun da baya sakinka idan kina tsoro, da kuma mutumin da yake maida duniya gaba daya ta yi shiru saboda ke. Private jet dinsu ya bar hamadar Amangiri ne da sassafe. Idanun akhnan kafe daga qasa. A qasan golden desert din na qara nisa a hankali. Amma duk da tafiyar,akhnan har yanzu tana kallon wajen ta window kamar bata son barin peace din da suka samu a can ita da haisam din. Yana zaune kusa da ita. Suit dinsa dark charcoal. Ta kalli hannunsa a hankali,agogon hannunsa na kyalli under soft cabin lights. Wannan royal calm dinsa ya dawo yanzu. Phones. Business calls. Security updates,kamar da zarar sun bar Amangiri duniya ta sake tunawa da shi. Wannan ya sake gaya mata da gaske ya manta da kowa dake duniya sanda suna Amangiri. Da gaske ya bar mata dukka duniyarsa ne da lokacinsa gaba daya. Ya sadaukar mata da komai da komai ita daya!. Sai dai ta lura duk tsakiyar calls din,idanunsa na komawa kanta lokaci zuwa lokaci. Always checking. Always aware of her. “You’re back to being busy.” ta fada softly cikin salon tsokana. Wani lallausan murmushi ya saki yana sauke wayar dake riqe a hannunsa. “I was always busy.” “I just ignored the world for you.” wani laushi zuciyarta tayi, ta lumshe idanunta a hankali. Kowacce magana Idan zaiyi sake bata proof yakeyi na yadda yake qaunarta. Kowacce magana proof ne na yadda soyayyar ta take da zurfi a zuciyarsa. Da wannan kallon yake dubanta, da wadannan idanun nasa masu matuqar kwarjini. Idanun nan da har yanzu nauyi suke mata. "Zo nan" Ya fada softly yana miqa mata hannunsa. Ka fada ta maqale tana narke idanunta cikin nasa. Jikinsa ya mutu murus da kalar kallon da take masa. "Ayimin izini ranki ya dade na qaraso idan ba zaki samu tasowa ba" ya sake fada yana karya wuya kamar wani marayan da ya rasa uwa da uba gaba daya. Murmushi ne ya subuce mata, ta karyar da wuya itama tana kallonsa. Tana kallon mutumin da dukka rayuwarta da numfashinta suka dogara dashi. Sai ta miqe, da wata irin nutsuwa,da wani irin taku da tasan yana janye hankalinsa. Da wani irin yanayi da takejinta a sama. Tana jinta kamar tafi kowacce mace sa'ar miji da dacewa. Kyakkyawan masauki ya mata cikin jikinsa,yana matseta da kyau a jikin nasa. Ya sauke wata sassanya kuma siririyarr ajiyar zuciya yana cewa. "duk sanda nake neman gida......ba wani gida sama da nan" ya fada yana nuna saman qirjinta,inda mafi yawan lokuta a nan yake kwantar da kansa idan zai mata runguma irin wannan. Hannuwanta duka biyun ta saka itama tana zagayeshi gami da rungumeshi tsam cikin jikinta. T sauke itama ajiyar zuciyar tana bashi daman sakewa a jikinta. Lokuta da yawa bata iya magana,bata iya cewa komai idan ya soma dafa zuciyarta da lausasan kalamansa irin haka. Lokacin da suka isa jimma sama ta fara duhu kadan da alamar samun saukan ruwan sama kowannw lokaci daga sannan. Jimma ta yi green sosai saboda wadataccen ruwan sama da tsirrai suka samu. Gari ne da yake da wani irin yanayi me kyau tun asali,wadatar shuke shuke da qoramu dake sanya garin kasancewa cikin koren yanayi,sosai suke da yawaitar tsirrai,tsaunika masu kyau dake qarawa garin kyau,bishiyoyi dake dashe a tituna da Street na anguwanni. Wani iska mw sanyi garin yake bayarwa,ga qamshin qasa mai sanyi dake alamta saukar ruwa. Convoy mai tsawo ne yake jiransu outside private airstrip. Black luxury SUVs,royal security. Mutanensu ne cikin girmamawa da Karramawa. Zuwa yanzu ta gama fahimta ta kuma fara sabawa da ganin komai tattare dashi......amma kowanne lokaci tana sake fahimtar haisam ba ordinary bane. Soyayyar mutanensa a kansa tana da girman data isa ka gane cewa,bawai.....sun sonsa bawai don yarimansu bane. Suna sonsa bawai don ya mallaki dukiya bane. Aah,kalar soyayyar da suke masa.....soyayya ce da zakasan cewa tausayi da kulawa da kyautatawa sune jigon ginata. (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) A nutse giiftii akhnan ta sauka daga motar tana kallon surroundings din sans motocinsu ke daukan hanyar gida. Wannan bangaren Jimma din da suke nufa ba irin city din da ta sani bane. A hankali ta waiwayo gare shi tana dubanshi. "ina zamu je?" ta furta kai tsaye,don ita nanay takeso ta gani,ta masu taje ta ganta. Har cikinranta da zuciyarta takejin tayi missing dattijuwar sosai. Sosai take jinta a ranta tamkar mahaifiyarta. Ko ba komai......ko ba alaqa ai ta haifa mata jarumin maza,daya tamkar da Million. Siririn murmushi ya bayyana a lips dinsa. Wancan murmushin nasa nan da yake nuna ya san wani abu ita bata sani baa “Home.” ya amsa mata a taqaice. "wanne gida......banga nanay ba.....haisam mana" ta furta a shagwabe tana kyabe fuska. Murmushi ya kuma saki,yana lumshe idanunsa gami da budesu duka lokaci guda. Har jijiyoyinsa yake jinta idan ta kirayi sunanshin nan. Baisan sai yaushe ba,bausan sai yushe zai daina jin dadin sunanshi idan ta kira ba.... Ba lokaci,baya jin akwai zuwan wannan lokacin. Sai ya gyada kai kawai yace. “Mhm.” “The one I built for you....Ba wani guda bayanshi akhnan" Ya fada yana lumshe idanunsa Akan fuskarta. Zuciyarta ta motsa a hankali. Yau itama zata shiga gidanta kenan Kamar kowacce cikakkiyar mace?. Idanunta ta maida a hankali kan hanya sanda motocinsu suka fara hawa wani private mountain road. Fog mai laushi na zagaye da bishiyoyin gurin. Tun daga tsarin hanyar da titin tasan cewa wata unguwa ce...... Wani guri ne na musamman da yasha banban da kowacce hanya.... Kowanne titi da kowacce unguwa. Tsarinsa na dabanne kuma na musamman. Tun daga nutsuwa da shirun titunan. Kwaltar da aka malale titin dashi,dama fitilun dake jere tare da shukokin da suka yiwa titin rumfa. A hankali suka fada wani street daban na cikin unguwa, Wanda duka duka tafiyarsu bata haura mintuna goma ba zuwa sha biyar suka soma qoqarin tsaiwa gaban wata villa. Idanunta ta daga a hankali,kyawawan idanunta nan da suka qara girma da haske tana saukesu saman Villa din da yake a gaban ta din,daidai sanda motocinsu suka fara motsawa a hankali suna shigewa ciki bayan tafkeken gate din gidan ya bude Kansa da kansa automatically ba tare da kowa ya isa gabanshi ko ya tabashi ba. Ba kawai gida bane. Masterpiece ne. Modern royal architecture. Huge glass walls. Dark stone exterior. Soft warm lights. Gidan ya zauna cikin mountains kamar wata boyayyar masarauta da aka killaceta daga ganin idanuwa. Water features na gudu softly a gefe. Dogayen bishiyoyi sun kewaye compound din. Everything private. Everything expensive. Wani irin laushi jikinta yayi,taji wani irin nauyi yana ratsata. Wanna irin gida ne wannan kenan?. Wacce irin ginanniyar masarauta ce?. Me yasa komai nata yakan sanyashi ya zama na daban?,me yasa ko yaushe yake zabar mata surprise akan komai?. Da wannan halin nasa na basarwa.... Yayi abinda ya kamata ya kalleka..... Yayi abinda ya dace ya tsaya ya tayaka dauka girman mamakin abun,Amma sai yayi burus Kamar baisan komai akai ba. Tafin hannunsa ya bata sanda kowanne guard da security na gidan suka janye suka kuma juya baya don bawa matar oga daman fitowa. Idanunshi ta sake kalla,har yanzu bai yarda ya kalleta ba, Amma tana iya ganin kyakkyawan murmushi can qasa boye qasan idanunsa. Ta janye nata idanun tana dora masa nata hannun kawai saman nasa ba tare da tace komai ba. *zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 08187255862 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 08187255862 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽 💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 141* ___________________________ *_Amintaccen gurin siyayya_* *_ingantattun kaya akan ingantaccen farashin da ba irinsa a kasuwa_* *_BONONZA DA PROMO akai akai_* *dukka sai a HUGUMA CLOSET* *Duniyar kayan yara,mata,maza,dukka* *shaddodi,atamfofi,laces,abayas,jakankuna,takalma,agogo,sarqoqi,English wears,night wears,under wears,da duk wani nau'in sutura babba da qarami* *_Karki yadda ayi babu ke.....leqa kiga yadda closet din HUGUMA kullum ke cike da kaya akan farashi me kama da KYAUTA_* *_YAN SARI....YAN REPOSTING.....DA SARAKAN ADO MASU SIYA DON KANSU....DUKKA INA MUKU MARABA_*🤝🤝🤝🤝 https://chat.whatsapp.com/FrqgC0YmUWP4FPmUzYuLJX __________________________ Cikin girmamawa ma'aikata da hadimai na gidan ke miqa musu gaisuwa,cikin girmamawa da sunkuyar da Kai. Wani irin ban girma da har yanzu yake saukar da mamaki a zuciyar akhnan. Da kulawa Kamar ba wannan hamshaqin yariman billionaire din ba yake amsawa. Yana riqe da hannunsa cikin nata Kamar wanda za'a qwacewa ita Idan baiyi hakan ba. Tare suka ratsa cikin gidan,har suka kai deluxe entrance na gidan. Wata irin qofa da akhnan ta kasa gane kanta kwata kwata,sai idanu da take binta dashi. Yadan sunkuyo kadan zuwa fuskarta. "Kiyi addu'a" Ya fada a nutse,ta lumshe idonta tana sauke ajiyar zuciya. Komai matsayinka a rayuwa akwai na gaba dakai. Da gaske ne baba ma da babansa, tabbas rayuwa ta gaji irin wannan abubuwan. A nutse yake Karan to mata addu'o'in tana maimaitawa, ya sake riqe hannunta cikin nasa suka sanya qafafuwansu bakunansu dauke da bismillah. A cikin jikinsa ya sanyata, suka fara zagaya gidan ita dashi yana mata bayanin kowanne sashe dalla dalla. Ta kasa magana,sai bin ko Ina kawai da takeyi da kallo. Duka yadda taga ginin daga waje, ta ciki ya zarta hakan. Wata aljanna ce kawai ya Samar da ita tun daga nan gidan duniya. “Haisam…” ta kirashi tana dubansa bayan daya Kira sunanta tana tsaye cikin dakin Yara. Wani irin daki da aka masa wani tsari na musamman, tsari me daukan hankalin da duk uwa zataso ace mallakin abinda zata Haifa ne. Komai an saka a dakin, ba wani abu da za'a buqata sai sanda za'a haifi abinda aka tanadi gurin saboda shi. “You like it?” ya tambayeta, yana tsaye da wannan tsaiwar tasa irin ta giant din maza. Hannunsa zube cikin aljihun wandonsa ya rusunar da narkakkun idanuwa nan nasa a kanta. Ta kasa magana ma kwata kwata, Idan ta bude baki zatayi magana sai taji muryarta tana rawa. A hankali ta fusgo kalmar “You built this?”Sai ya gyada kai. “For year” Ta kasa magana kawai tana lissafa kwanakin zuwansa agadez. Shekara ta farko daya fara saninta. Shekarar daya fara hada idanu da ita. Shekarar daya fara jin cewa yana sonta a rayuwarsa. "A wannan shekarar kenan ya fara gina gidan saboda ita? " Ta yiwa kanta tambayar tana daga idanunta tana zubesu a kansa. Yanzu take sake realizing.....tun kafin abubuwa su kai yadda zasu fara magana da juna.....tun kafin ta fahimci yadda yake sonta.....already yana gina mata future cikin wannan shirun daya zama tambarinsa. "Amma wannan dakin...... Bani da ciki haisam" Tayi maganan tana narke murya. Murmushi ya saki,wani qaramin murmushi me dauke da tarin ma'anoni. Baisan ya mata suke idan suka samu ciki ba, Amma shikam lamarin akhnan dariya yake bashi. Har yau har gobe taqi believing abinda takeji,bayan ita kanta shaida ce da yadda abubuwanta keta canzawa. Ita kanta shaida ce Akan yadda komai nata yake tafiya ba'a daidai ba, ba'a kuma yadda ta sanshi ba. "I know" Kawai yace mata, yana qoqarin adana dariyarsa. Taku biyu ya iso gabanta,ya sake sanya hannunsa yana lalubo hannunta cikin nasa, ya hade tafin hannunsa da nata, sannan ya fara takawa da ita a hankali suna fita a dakin. Juyawa take tana kallon komai cikin disbelief. Ta tsaya tsakiyar living area din da suka sake bullowa. akwai elegant staircase,saidi amma ba sama yake hawa ba. Qasa yake sauka,underground. Ta sake maida idanunta kansa da mamaki. “What’s down there?” ta zabi ta bayyana qauyancinta kawai akan tayi shurun. Haisam ya zuba mata ido,siririn murmushi yana subucewa daga labbansa. Tana burgeshi, bata da girma kan nuna batasan abu ko bata ganeshi ba. Zata tambaya ne Kai tsaye kawai, ya danganta da yadda ka dauki abun. “Come see.” ya kamo hannunta gently. Sauka suka fara yi tare,step by step. Wasu irin soft hidden lights na cikin stairs din na haska ko Ina, har saman qafafunsu da suke takawa da wata irin cikakkiyar nutsuwa. Akhnan na jin zuciyarta na bugawa saboda gidan already ya wuce imagination dinta. "To me zai sake boyewa a qasa?" Ta tambayi kanta da kanta can qasan zuciyarta. Ko ba'a fada mata ba stair case din ta musamman ce. Kana takawa kana jin wani sanyi da taushi qasan tafin qafarka. Suna sauka suna nutsawa zuwa qasan wani yanayi me dadi yana lullube gangar jikinka. Wani haske.... Wani tattausan oud scent me dadin shaqa. Da suka isa qarshe sai ta tsaya cak. Gaba daya underground level din kamar secret luxury world ne. Private indoor lounge,glass ceiling sections,soft waterfall wall,library,cinema room ga kuma hidden relaxation spaces haka suka dinga zagayawa daki daki. Kamar wajen da mutum zai boye daga duniya ya samu sukuni ya manta da komai. Sai a sannan ta sake gasgatawa,ta sake yadda dashi. Da gaske bayason hayaniya. Da gaske shi din mutum ne da baison dogon zance ko kuma hayaniya ko kadan. Tasha jin su rumaisa suna gulmarsa,amma yau ta samu tabbaci da kalan ginin gidan qasan da yayi. Ta juya gare shi cikin mamaki sosai,sai ya sake bata hannunsa suna sake takawa ciki. Da suka shiga ciki,even the silence felt luxurious. Huge open spaces. Warm lighting,minimalist elegance....Oud scent mai laushi. Kowane detail din wajen carefully planned ne. Da wannan nutsuwar tasa..... Tsarin nasa da ita aka gina wajen..... Da ita aka gina komai na gurin. “This doesn’t even look real. " Kaman bazai magana ba, kaman bazai motsa ba kafin ya tako a tausashe ya qaraso kusa da ita sosai. Kusan da take iya jin saukar numfashinsa a hankali. “It’s real.” yadan dakata da tarin nutsuwarnan tasa. “And it’s yours too.” wani irin shuru ya gilma,akhnan ta ji zuciyarta na yin wani irin laushi,saboda duk inda yake kai ta.....bawai wajen nuna kudi kawai yake kai ta ba,a'ah... Yana gina mata tsaro da wani irin aminci ne,da rayuwar da bata taba mafarkin zata samu ba. Ta bude baki zatayi magana,Amma sai ya hana mata wannan damar, ya sanya hannuwansa gaba daya ya daga ta cak ya rungumeta a qirjinsa yana cewa. "Ki huta haka nan,zan amsa kowacce tambaya taki bayan kin huta" Wani guri taga yana nufa da ita, sun wuce wani dogon guri me kama da hallway wanda ya qunshi wasu irin luxury bedrooms ba daya ba ba biyu ba. Ya zabi daya daga ciki ya tsaya a gaban qofar, tayi magana cikin harshen turanci tana nuna fahimtar waye tsaye a wajen, ta kammala scanning nasa ta bude musu suka shige. "Welcome to my world" Ya furta yana direta tsakiyar bedroom din data jita tun bayan shigowarta tana fita daga duniyarta zuwa wata duniyar ta daban. (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) Gaba yayi zuwa wata qofa kawai ya barta, duk yadda taso ta maze kuma ta kasa, sai data saki idanunta sosai tayi kalle. Kalle yadda ya kamata. Ta sauke ajiyar zuciya a hankali, sai ta samu kanta da furta. "Alhamdulillah" Don a yanzun bata da sauran abinda zata yiwa Allah Idan ba godiya ba. Ya bata sama da yadda ta tsara..... Me yafi wannan ni'ima da dadi ga ubangijinka?. Ruwan wanka ya hada musu,kaman kuma yadda ya tsara wankansu a tare Tun a wancan ranar ba abinda ya sauya wannan tsarin. Tare suke wanka, ba wanka kawai ba komai da komai ma. Har wani lokaci tana tunanin,ya zaiyi Idan aiki ko tafiya ta sameshi ba tare da ita ba?. Duk da shi kawai take tunawa tana mantawa da kanta,wanda tasan zata fishi jigata tabbas a yanzu Idan wani abu da zai sanya suyi nesa da juna Idan ya taso. Idanu ya zuba mata ganin yadda taqi cin komai cikin abincin da aka shirya a gabanta. "Habibty" Ya Kirata da wannan muryar tasa da sautin ke ratsata a duk sanda zai kirata. Idanunta ta daga a kansa, Shima ya mata nuni da taci wani abun. Fuskarta ta bata, ita kwata kwata ba abinda yayi mata, batasan yaushe ta canza ta koma haka ba. Tana jin cewa Tana son cin abubuwa da yawa, amma komai Idan an kawo sai taji ya fita daga kanta. Har tausayinsa takeji sometimes, sai taga Kamar tana bashi fatigue ne kawai. "Nanay nakeson gani please" Ta fada da shagwabar nan tata. Numfashi ya sauke a nutse, yana jiye spoon din hannunsa idanunsa cikin nata. "Please.....kada kace a'ah" Ta furta tana hade hannayenta guri daya. Kaman bazai magana ba, sai a hankali ya furta. "Okay" Da wani sauti can ciki. "Ya Salam" Ta fada can qasa,simplicity dinsa yana burgeta sosai. "Na gode yarima na" Yadda ta fadi maganan ya sanyashi sakin murmushi me qaramin sauti. "Ni ba wannan cin hancin nakeso a bani ba, already na sani yarima ne ni...... Cin hancina...... Na dare nakeso. A wannan sabuwar duniya,DAGA NI SAI KE" Ya qarasa fadi idanunsa suna narkewa cikin nata. "Baka da damuwa" Ta fadi da wani irin confidence tana rolling idanunta, abinda ya kusa zautar dashi, ya sanyashi miqewa yana ture plate din abincinsa. "Let's go" Dariya sosai ta saki har tana duqawa saman table din, sai ya koma baya a nutse ya tsaya yana crossing hannayensa a qirjinsa,sannan yayi crossing legs dinsa yana qare mata kallo. "Ni kike wa dariya giiftii? " Ya fada da softness dinsannan yana nuna kansa da yatsarsa. "D'okin is too much my prince" Idanunsa ya lumshe yana budesu, sai ya sauke hannayen nasa da qafafunsu qasa, ya soma takawa zuwa gareta. "Okay..... Lemme show you irin d'okin da nake" Tana zullo tana komai haka ya dagata cak ya wuce bedroom din da ita. Sai daya goge mata duk wata hadda ta kanta tas. Ya jefata wata duniya data sanya ta dinga leqen fuskarsa bayan wani dan gajeran bacci yayi awon gaba dashi. Ta miqa hannu a hankali ta saka dan yatsanta qwaya daya tana maida sumarsa data kwanto gaban goshinsa zuwa baya. Ya mata wani irin kyau,kamanninsa sosai dab da ita. Allah ya sani,bata taba ganin namiji me wani irin kwantaccen kyau irin nasa ba. Komai nasa me kyau ne,komai nasa me wani irin sanyi ne da daukan hankali. Ta dan matsa kusa da shi kadan. Idonta ya sake tsaiwa a kansa. Wani lokaci har yanzu bata yarda cewa wannan mutumin… wanda mutane ke tsoro saboda kwarjininsa ba.....wanda wanzuwarsa kawai ke sa mutane su yi shiru…. Shine mutumin da yake jan blanket ya lullubeta idan taji sanyi. Shike hada shimfidata da ita. Shike gauraya numfashinsa da nata numfashin. Ta bi fuskar tasa da kallo a hankali. Dogayen lashes dinsa, dogon hancinsa, kwantaccen sajen dake qasan habarsa.....hannunsa da yake kusa da nata,sai murmushi mai laushi ya bayyana a fuskarta ba tare da ta shirya ba. Ta sauke ajiyar zuciya a hankali tana janye yatsanta. Caraf taji an kama yatsan an riqe, sannan a hankali ya bude idanunsa ya zubesu fes saman fuskarta. Ba abinda yake tunawa sai duniyar data jefashi a dazun,wata duniya da yake fatan har abada ta zama mallakinsa shi da ita. *zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 08187255862 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 08187255862 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 142* _________________________ https://chat.whatsapp.com/BkfPzSEDhnsIwyCD8LNGkm?s=cl&p=a&mlu=0 *IDAN KINSAN BA ORDER DIN KAYA ZAKI DINGA SAKAWA BA* *IDAN KINSAN BA BUSINESS KIKE DA NIYYAN YI NA KAWO KAYA DAGA CHINA BA KARKI SHIGA* *_DON ALLAH KARKI BATAWA KANKI LOKACI_* *_Assalamu alaikum my loyal people_* *_Barkanmu da wannan lokaci,kuma barkanmu da warhaka_* *_akwai da dama cikin mata wadanda suke sha'awar yin order kaya daga CHINA zuwa NIGERIA,NIJER,CAMERON,CHAD da GHANA_* *_Amma rashin samun amintaccen company....ko hannun wanda zasu dinga siyan kaya ta hannunsu cikin aminci ya hanasu_* *_To a yau addu'ar da yawa daga cikinku ta amsu,don nayo muku tsarabar kamfanin da zakuyi siyayya ta hannunsu su kuma dora muku kayanku har qasarku cikin aminci ba tare da fargaba ko d'ar d'ar ba_* *_kunsan komai nawa TASTED AND TRUSTED ne,to wannan kamfanin idan akwai abinda yafi TASTED AND TRUSTED ma shine_* *_Baki da fargaba kota sisin kwabo,ni SAFIYYA HUGUMA na tabbatar da hakan_* *_Zaki iya kasancewa dasu group nasu,inda a nan zaki hadu da agent dinsu da CEO nasu gaba daya ta wannan link din,zaki samu bayanansu da komai da ya shafi mu'amala dasu_* *INA ME BAKU TABBACIN AMINCI DA INGANCI DA SAUQIN MU'AMALA DASU DA IZININ ALLAH,BAN TALLATA MUKU SU BA SAI DANA GWADA* *Allah ya dafa mana,yasa mana albarka a nemanmu,ya albarkaci halal dinmu ameen summa amee* __________________________ "How long have you been staring at me?” ya fada da muryar bacci,wata nannauyar murya me ratsa zuciya sosai idanunsa suna lumshewa,Adams Apple dinsa yana sama da qasa Kamar me hadiyar wani abu. "Ban.... " Ta fadi tana zaro idanunta saboda ya shammaceta. "You’re a terrible liar.” Ya fada da wannan nannauyar muryar tasa idanunsa a kan razanannun idanun nata. Ta masa wani irin kyau, musamman sanda ya fadi hakan, ya kuma sanyata kauda Kai gefe kunya tana cikata, sai ya jawota sosai softly cikin jikinsa sanda take amsa masa. "Na dauka bacci kakeyi" "I was" Ya amsa mata a taqaice yana kissing dogon wuyanta gami da sake mannata a jikinsa. "Then why did you wake up?” ta fada a shagwabe tana turn baki gaba. A hankali wani lazy smile ya bayyana a gefen bakinsa, ya gyara mata kwanciya sosai yana shaqar qamshin hair mist dinta "I felt you..... Shi yasa na farka"wani shuru ya ratsa tsakaninsu,tana qoqarin qidddige yawan adadin soyayyar da yake mata,wadda takai har cikin baccinsa ma yana iya feeling presence dinta. "Tell me" Ya sake fada da wata sirrintacciyar muryar data kasance tata ce ita kadai. Ita kadai kejin wannan sautin....... Wannan muryar da wannan amon. Ta lumshe idanunta tana jin yadda muryar ke saukar mata da kasala a kowacce gaba ta jikinta. “I was thinking…” sai ta dakata “…you look peaceful when you sleep.”ta qarasa fada tana sauke idanunta da wani irin sanyi akan fuskarsa. Kallon yaji yana ratsa shi a hankali,kamar wanda aka mannawa qanqara a qirjinsa. Shuru, wannan shurun dai ya sake ratsawa ta tsakaninsu, kaman bazaice komai ba, sai kuma ya dora hannunsa a hankali yana rarraba dogayen eye lashes dinta. Ya motsa labbansa a hankali da wata irin kasala. "That’s because my heart rests when you’re near me.” wani irin abu ke sake sauka a zuciyarta, tana jin yadda zuciyarta ke bugawa..... Saboda shi kadai. Sai ya sake zuba mata ido cikin sleepy softness din nan tana sake yi masa kyau. "You watch me like you’re scared I’ll disappear.” ya fada yana lakace mata hanci. "You disappeared once already.” ta fadi tana cizon fatar qirjinsa a tausashe. "Ouchch" Ya fada Kamar da gaske yaji zafin cizon, sai suka saki dariya ita dashi gaba daya lokaci guda. Sanda suka gama shiryawa ji yayi kaman yace su fasa zuwa gurin nanay din. Ya dinga qare mata kallo,tun daga siffa har zuwa takunta. Ya ware mata hannunsa yana sauke mata lallausan murmushi. Batayi qasa a gwiwa ba ta qaraso ta shige ciki, tayi luf abinta tana sauraren bugun zuciyarsa. Sai da suka kusa minti goma a tsaye a haka ba tare da yace mata komai ba,sannan ya janye ta a hankali yana kissing goshinta. Wannan yanayin ba wani sabon abu bane a wajen ta. Ta riga ta saba da hakan,sometimes yakan zabi gaya mata abinda yakeji a kanta ta hanyar runguma,sanyata cikin jikinsa da bata daman sauraron bugun zuciyarsa sama da magana da baki. Sanda suke takawa a farfajiyar gidan, riqe da hannuwan juna. Kai me karatu inda zaka hangensu a sannan zasuyi matuqar burgeka. Yariman Jimma da sarauniyar agadez. Wani iri perfect match ne da yake bawa kowa mamaki. Ba iya mutanen waje ba. Daidai da ma'aikatan cikin gidan wani lokaci suna labewa satar kallonsu. Kamar ko yaushe,ya bude mata motor da kanshi, sannan ya zagaya daya bangaren shima ya shiga. Motor ta fara motsawa tana barin gidan. Idanunta akan farfajiyar gidan, komai tana ganinsa da wani irin yanayi me matuqar jan hankali, komai na gidan burgeta yakeyi,hakanan komai din sai yake mata kamar dama can ita ta zauna ta tsara yadda komai zai kasance a cikin gidan nata. Sanda suke shiga masarautar Jimma,abinda yafi bata mamaki basu sanar da zuwansu ba, amma kafin su wuce gate na farko har kowa ya ankara da isowar yarima haisam. Suna ta cikin motar ne basu kai ga fitowa ba,amma wani girma dukka hadimai da al'ummar masarautar ke bawa motar kanta bama su ba. Kowanne shinge da zasu wuce kafin sukai ga qarasowa ake budeshi da wani irin yanayi me cike da girmamawa. Shi ya sake bude mata motar, ya zagayo ya riqe hannunta yana fiddo da ita, sannan suka fara takawa zuwa cikin gidan yana amsa gaisuwar bayi da hadimai da wani irin yanayi dake nuna asalin izza da sarautar dake yawo a jininsa. Faluka bayan faluka suka dinga ratsawa shida ita. Tako Ina gaisuwa ce cikin girmamawa suke karbarta shi da Akhnan din. Sanda suke isa sitting room na qarshe da zai sadasu da inda nanay tafi zama,a daidai lokacin take shigowa itama ta daya qofar da ahalin gidanne kawai suke using wannan qofar, Kamar yadda yake akwai kebantattun gurare da iyasu dinne kawai ke da access da gurin. Ganin farko data musu taji wata matsananciyar faduwar gaba ta saukar mata. Wani irin kyau suka mata me daukan hankali. Kwarjininsu,da kalar matching din da sukayi da juna abune da idanu ba zasu iya kaucewa a kansu ba. Har tayi taku daya baya,amma wata zuciyar me cike da kishi ta bata shawarar dawowa. Ba musu ta tako a hankali zuwa gabansu. "Barka da shigowa obbo" Ta fadi da wani yanayi na girmamawa sosai cikin muryarta,da kuma nuna kulawa. Yanayin daya tafi a hankali,kai tsaye kuma ya sauka a zuciyar akhnan. "Yauwa" Ya fada a taqaice idanunsa suna kan hanya. Ta dan saci kallon akhnan. Ko yaya tana so tayi abinda zata qona mata rai,tanaso ko yaya ta motsa wannan izzar tata. "Kamar nanay tasan zakazo,tace na hada mata coffee me yawa na kawo mata" Ta fada da murmushi a fuskarta tana dubansa. Abun yadan masa banbarakwai,amma hankalinsa sam baya ta gurin,sai ya waiwaya yana duban akhnan din. "Mu qarasa?" Kai ta gyada masa a nutse,sai ya sake ware hannayensa yana sarqesu da nata kamar wanda akace za'a qwacewa ita. Akan idanunta yayi hakan,bata sare ba ta murmusa kadan. "Idan ba damuwa na maka iso,kaman ta zauna zaman addu'a" Ta fada da girmamawa,amma yadda tayi gaba ba tare data damu da miqa wannan girmamawar ba yaja hankalinsa. "Saamee" Ya kirata kai tsaye. Har cikin ranta taji saukar sunan,wani abu me sanyi ya lullubeta,don ta manta yaushe ne na qarshe da taji ya kira sunanta. A ladabce ta waigo tana amsawa. "Wannan ya zama karo na qarshe da zakiga matata ki wuceta ba tare da kin gaidata ba.....ina fata baki manta hukuncin dake kan duk wanda ya aikata hakan ba". Wani irin qasqanci zallarsa taji yana mamayarta. Wannan maganar tasa tana daidai da tuni daya mata gami da maidata asalinta na DIYAR BAYI. kenan....hakan na nufin ba'a canzawa tuwo suna?. Hakan na nufin ita ba diyar kowan kowa bace har yanzu ba abinda ya shafe wannan?. "In sha Allah" Ta fada a sanyaye,sannan ta waiwaya sashen akhnan. "Barka da isowa" "Na gode" Akhnan din ta amsa still ba tare daya dubi sashenta ba. Wani abune ya mata tsaye a zuciyarta,wasu irin dabi'u take karanta tattare da saame wadanda suke bata haske kan inda ta nufa. "Ba buqatar kiranta....zan qarasa da kaina" Akhnan tace da saamee sanda take shirin isa ga nanay ta sanar mata isowarsu. Saita tsaya cak tana jin kamar an sace mata gwiwa,sannan taja baya a hankali sanda akhnan ke tattakawa riqe da hannun haisam ba tare data sakeshi ba. Dole taja gefe ta basu hanya,sannan ta koma da baya a hankali tana barin gurin. Suna shiga ta zame hannunta daga nasa,saita ja baya kadan tana duban idanunsa. Haka kawai ta samu kanta ta watsa masa harara. "Ban yarda kowa ya shiga tsakanina da sultane ba.....wai har don saboda inason ganin mahaifina sai anmin iso.....haka yake game da nanay. Ban gayyaci kowa gurin neman iso kan ganin mamana ba" Ta qarasa fada tana sake miqa masa wata hararar sannan ta fara takawa. call "Tun wuri ka gaya mata. Bakin rijiya ba gurin wasan makaho bane....idan da wani tunani da take dashi a kanka,ka gaya mata ta daina,tun kafin ta shiga inda ba zata iya fitowa ba" Ta dan matsa kusa da shi, idanunta cike da kishin da take qoqarin boyewa. "Tana kirawa kanta tashin hankalin da mutane duniya duka basu isa mana sulhu ba" (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) "ni khadeeja muhammad hammud ba sa'ar kowa bace". Wani lallausan murmushi ne yake fita ta gefan bakinsa,idanunsa zube fes a kanta. Idan tana nuna kishinsa irin haka,shi kadai yasan yadda abun ke burgeshi,shi kadai yasan yadda abun ke masa dadi. Hararsa ta qara yi,yanayin daya sanya idanunta suka masa kyau. "Kaima kada ka sakemin wannan murmushin" "Which smile?" Ya tambaya cikin nutsuwa kuma kai tsaye still yana kallonta. "Wanda yake nuna jin dadin abinda nake fada" Ta sake fadi wannan karon harda murguda masa wannan qaramin bakin nata. Dariya ta kusan subuce masa,yadda ta koma me tsiwa sosai cikin lokaci kadan. Wannan tsiwar da yake hange daga nesa.....yau gata kusa dashi ana gwada masa. "You're jealous" Ya fada murmushinsa yana qara fadada. A hankali ta bude bakinta don ta musanta,amma saita kasa hakan,ta kauda kanta gefe tana tura baki gaba. "Duk yadda ka dauka" Sai ta fara takawa zuwa ciki. "Akhnan." Ya kirata yana jin yadda idanunsa suke narkewa a kanta. Ba tare da ta juyo ba ta amsa. "Me kuma?" "Kin makara." Ta hade gira. "Makaran me?" Ya jingina da bangon dake kusa dashi yana kallonta "Da wannan kishin." A hankali ya qara da fadin. "Da kin zo shekaru da suka wuce,da kin samu abin kishi." Sai ya girgiza kai. "Yanzu kuwa..." Ya dakata na dan sakanni. "Babu wanda nake gani sai ke." Akhnan ta ji yadda zuciyarta ta yi wata irin bugawa,amma duk da haka ta qi ba shi nasarar gani a fuskarta. Sai kawai ta sake jefa masa harara,wacce a wannan karon ta fi kama da murmushi fiye da fada,ta kuma juya abinta tana shigewa zuwa ga nanay. Cikin nutsuwa ta yiwa nanay cikakkiyar sallama,nanay din dake saman abun sallah rumaisa a gabanta da alama magana suke ta amsa tana d'aga kanta zuwa ga akhnan din. Wani faffadan murmushi me cike da qauna da soyayya ya kubcewa nanay din. "Giiftii.....fitowa kikayi?,haisam bai gaya miki zanzo da kaina na ganku ba?" Nanay ta fada cikin kulawa tana duban akhnan da tarin soyayyar da irinta takewa mahaifiyarta safeena. Qasa akhnan din tayi da kanta,tana jin wata matsananciyar kunyar nanay da bata taba jin irinta ba. Haka kawai takejin all over her body nanay na ganin komai. Komai da sukeyi ita da haisam din,dama yadda haisam din ya lalatata a kwanakin nan. Ashe haka surukutar take?,take tambayar kanta sanda takejin ba zata iya hada idanu da nanay ba sanda nanay din ta miqe da kanta tana marabtarta. "Maraba da diyata" Nanay ta furta tana budewa akhnan hannuwanta don ta rungumeta. Idanun nanay din a kanta sanda take takowa,mamaki kadan yana kama nanay din da yadda akhnan din ta wani bude lokaci guda tsakanin tafiyarsu da dawowarsu. Ta sauya gaba daya kamar sai a yanzunne mijinta ya santa diya mace. Wani abu ya d'arsu a zuciyar nanay din sanda take rungume akhnan a jikinta. "Barka da warhaka nanay" Ta fada tana rusunawa cikin jikin nata. Riqeta tayi sosai a jikinta. "Banason ganin wanna surukutar cikin idanunki giiftii.....ke din kamar rumaisa kike ko Aanani,matsayinki ma a zahiri ya d'ara wannan" Ta fada tana dagata daga jikinta gami da mata mazauni saman shimfidarta data tashi a kai. Rumaisa na zagayowa tana zama gefan akhnan din gami da leqen fuskarta sosai. Ita kanta mamakin sauyawar giiftii din tasu takeyi,wani ajiyayyen kyau tayi me matuqar daukan hankali duk da tarin kyan nan nata. "Giiftiin Captain.....kina kallon madubi kuwa?,anya captain sheikh zaici gaba da barinki fita koda tare zaku fita din?" Ta tambaya da gaskiya cikin muryarta. Ture hannunta kadan akhnan tayi cikin jin kunya tana mata nuni da nanay da idanu. Nanay din da tayi kaman bata ji ba,saidai zuciyarta tayi nisa a wani tunani. *zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 08187255862 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 08187255862 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 143* ________________________ https://chat.whatsapp.com/BkfPzSEDhnsIwyCD8LNGkm?s=cl&p=a&mlu=0 *IDAN KINSAN BA ORDER DIN KAYA ZAKI DINGA SAKAWA BA* *IDAN KINSAN BA BUSINESS KIKE DA NIYYAN YI NA KAWO KAYA DAGA CHINA BA KARKI SHIGA* *_DON ALLAH KARKI BATAWA KANKI LOKACI_* *_Assalamu alaikum my loyal people_* *_Barkanmu da wannan lokaci,kuma barkanmu da warhaka_* *_akwai da dama cikin mata wadanda suke sha'awar yin order kaya daga CHINA zuwa NIGERIA,NIJER,CAMERON,CHAD da GHANA_* *_Amma rashin samun amintaccen company....ko hannun wanda zasu dinga siyan kaya ta hannunsu cikin aminci ya hanasu_* *_To a yau addu'ar da yawa daga cikinku ta amsu,don nayo muku tsarabar kamfanin da zakuyi siyayya ta hannunsu su kuma dora muku kayanku har qasarku cikin aminci ba tare da fargaba ko d'ar d'ar ba_* *_kunsan komai nawa TASTED AND TRUSTED ne,to wannan kamfanin idan akwai abinda yafi TASTED AND TRUSTED ma shine_* *_Baki da fargaba kota sisin kwabo,ni SAFIYYA HUGUMA na tabbatar da hakan_* *_Zaki iya kasancewa dasu group nasu,inda a nan zaki hadu da agent dinsu da CEO nasu gaba daya ta wannan link din,zaki samu bayanansu da komai da ya shafi mu'amala dasu_* *INA ME BAKU TABBACIN AMINCI DA INGANCI DA SAUQIN MU'AMALA DASU DA IZININ ALLAH,BAN TALLATA MUKU SU BA SAI DANA GWADA* *Allah ya dafa mana,yasa mana albarka a nemanmu,ya albarkaci halal dinmu ameen summa ameen* __________________________ "Ina ya tsaya shi muhammad din?" Nanay ta tambaya tana zama sosai saman shimfidartata,saidai tana sauke maganan muryarsa ta bayyana. "Yaya za'ayi ki ganni nanay.......gani nan a tsaye kusan minti nawa.....amma nanay wai baki ganni ba tambayata ma akeyi" Ya fada da wani yanayi daya sanya rumaisa sakin boyayyar dariya. Murmushi nanay ta saki,tasan kishinsa da yadda bayaso a shiga tsakanin soyayyarta da shi. "To qaraso mana" Ta fada tana daga masa hannu. Kafada ya maqale yana komawa wani kalan tausayi. "Alqawari nanay......nima na cancanci a marabceni" Murmushi tayi ta kauda kai. "Ka shigo muhammad" Ta furta,sai ya tsugunna ya zame takalman qafafuwansa sannan ya sanyo qafar tasa a hankali yana shigowa. "Shikenan......tawa ta qare,Allah sarki ni" Ya fada da muryar tausayi wadda dukkansu sai data saka suka kusa fashewa da dariya,harsa akhnan da kadan kadan takejin yaren oromo,amma zamanta dashi tana fahimtar abubuwa sosai,maidawa ce saidai da qananun jimloli kuma. Ga mamakinta kanshi tsaye ya wuce saman abun sallar nanay din,ya qarasa zuwa gabanta ya zauna sosai yana tanqwashe qafafu. Hannunta ya kama cikin nasa,yana duban idanunta cikin kulawa da qauna ya fara gaidata. "Fatan kun dawo lafiya....." "Alhamdulillah nanay,ina fatan na same ki lafiya" "Lafiya qalau muhammad...." Ta fadi daidai sanda ya riqe hannunta yayi kissing bayan hannun nata. "Ma sha Allah" Ta fada itama tana dora hannunta saman nasa. Satar kallonsa akhnan keyi,mamakinsa yana saukar mata. Mutumin da kullum yake tafiya da cikakken iko da nutsuwa... wanda ko manyan mutane ke gyara zamansu idan ya shigo waje... yanzu yana zaune a gaban Nanay kamar qaramin yaro. "Amma muhammad me yasa baku zauna ta huta ba?.....nace da kaina zan shigo ko?,dazun muka gama magana da motii" Nanay ta tambayeshi tana kallonsa cikin zallar kulawa. Tunanin akhnan ya yanke sanda ya zame ya kwanta,yana dora kansa saman cinyar nanay din,ya gyara kwanciyarsa sosai fuskarsa tana nuna kalar nutsuwar daya samu. "Gata nan nanay....ita ta takura lallai sai tazo ta ganki" Ya qarasa maganan yana sanya idanunsa cikin na akhnan wadda mamaki ya sanyata daskarewa a gurin. Hannu nanay ta dora saman lallausan gashinsa "Laifinka ne......me zaisa ka bari tayi wahala.....halanma kaine ka matsa sai kun fito" Ta fada tana duban akhnan. "Wayyo ni" Ya fada a tausashe. "Nanay.....giiftii ta fara shiga tsakanin mu" Ya fada a narke yana maida idanunsa ga akhnan,akhnan din data narke a gurin tana kallonsa. Wannan ne haisam?. Wannan ne mutumin da idan ya shiga daki mutane ke gyara zamansu. Wannan ne mutumin da ko murmushi yake yi sai ya zama kamar ni'ima ga wasu. Amma yanzu...yana kwance kan cinyar Nanay kamar qaramin yaro da ya dawo gida bayan doguwar tafiya. Ido daya ya kashe mata,saita janye idanunta a hankali tana kallon qasa. A gurinta kawai da gurin nanay take iya ganin wannan siffar.....wannan kamannin.....da wannan haisam din. Mutum biyu ne kawai DUNIYARSA a rayuwa.....mutum biyu kawai ke iya ganin wannan side din nasa.....mutum biyu kadai,ita da nanay. "Zo nan kinji" Nanay ta fada tana miqawa akhnan hannu. A kunyace ta miqe tana matsowa gaban nanay din,wannan ya sake bata daman sake qarewa akhnan kallo sosai. Ta sauya....komai nata ya sauya,komai nata kuma yana bada wata alama ta daban. Amma ba wanda yace mata komai a cikinsu,wataqila kunya sukeji.....wataqila akwai sanda suka ajiye don sanar mata. Zata jira wannan lokacin,duk da bata da cikakken tabbaci. Cikin jikin ta zaunar da akhnan din,sai ya daga kansa a hankali yana dubansu,a badini zuciyarsa na masa wani fari da haske,yana kallon duniyoyinsa guda buyu,yana kallon farincikinsa.....aljannarsa da kuma rayuwarsa a fuskokinsu. Amma kuma a zahiri sai ya hade rai kadan. "Nanay....." "Haisam" Ta fada tana tsaidashi. Bayason kowa a gurin idan suna tare,ta sani,amma yanzun tana jin akhnan ta riga ta shiga wani bangare na rayuwarsu dukkaninsu. Kafin tace komai rumaisa data fice ta basu guri ta turo qofar. "Nanay.....an shirya table din" "Gani nan" Ta amsa mata,sai rumaisa ta juya ta koma,don sun saba kebewar Captain din nasu da nanay dinsa ba wanda ya isa ya shiga,sai yanzu da akhnan ta zama ta ukunsu. Tana riqe da hannunsu suka isa dining din. Katafaren dining din da aka shiryawa kalolin abinci,ba masu yawa sosai ba,daidai yadda zai nuna alfarmar wanda zai zauna cin abincin. Yana shirin jawa nanay kujera don ta zauna akhnan ta rigashi. Yadan fiddo idanu cikin subutar baki ya furta. "Easy mana....karki qara" Zuciyarsa nadan bugawa kadan. Gani yake kaman mistake qarami zai iya taba abinda akhnan din ke dauke dashi,abinda har yanzu akhnan din bata amince akwaishi ba. Dukkaninsu ita da nanay din suka kalleshi,idanun akhnan fal da tambaya,yayin da nanay kuma abun ya sake sa mata gamsuwa da zarginta,amma saita dauke kai kaman bata fahimci komai ba. Shima basarwa yayi yana shafa sumar kansa,ya matsa a hankali ya jawa akhnan tata kujerar,ta zauna,sannan yaja tasa opposite tasu shima ya zauna. Biyu daga cikin bayinta ne suka matso suka fara serving nasu,akhnan tana jin hirarsa da nanay din kadan kadan. Bata saka musu baki ba,duk da yadda nanay ke sakata a hirar. Yanayin mu'amalarsa da nanay na burgeta,har wani lokaci takan rasa tantancewa dawa yafi shaquwa?. Nanay din ko motii. Abu daya ta barwa ranta,shaquwa ce sosai tsakaninsa da nanay,da motii kuma wasu sirrikane yakeyi dashi wanda qirji da zuciyar uwa ba zasu iya dauka ba,dole lallai sai uban. (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) Fitowar noorah da Aareef ya sake sanyawa ta kuma jin dadin zaman. Tanason yarinyar sosai,tana da wani irin hankali me ban mamaki. Ta yarda ba banza ba haisam ke sonta shima. Tana murmushi take tsokanarta bayan ta gaidata. "Hoton me dame aka dauko mana a wannan satin?" Murmushi ta saki tana ciro camera dinta da bata rabo da ita. "Na sake siyan wasu sabbin tsuntsayen wajen halyjesheru ventures giiftii 704 666 5338....har da dawisu guda hudu.....kin gani" Ta fada tana miqa mata camera din. Daidai nan rumaisa da Aanani suka shigo,suka samu guri suka zauna suna jan plate suma,tana jin nanay tana mitar sai suqi cin abinci sai taxo cin nata,ta saki murmushi family din na sake burgeta. Tana murmushi tana duba hotunan,sai ta sake girmama lamarin ubangiji. Wasu irin kyawawan tattabaru da kaji,ga wasu irin dawisu harda parrot ma,ita sun mata kyau sosai,ta daga ido tana duban haisam. Girarsa ya dage mata,sai itama ta dage masa tata girar,ya juya ga noorah a nutse. "Auta,a saka mana order.....a zaba mata masu kyau" Murmushi noorah ta saki,wannan murmushin dake qarawa yarinyar kyau. "Amma obbo.....zan dora ribata fa" Murmushi ya saki "Riba halal ce auta,ki qara ko nawa kikeso" Suka saki dariya gaba daya. Duk cikinsu bayan shi itace ta biyu dake da neman na kanta sosai,shi yasa yake qara qarfafa mata gwiwa,yanayin abubuwanta zaka dauka ba daga gidan sarauta me girma irin wannan ta fito ba. Ga qananun shekaru amma haka take koyon kasuwancin dabbobin. Dauke da babban tray ta shigo gurin,ko sau daya akhnan bata yarda ta kalleta ba. Haka kawai batason koda ganin fuskar yarinyar. Ta qaraso tana tafiya a hankali zuciyarta tana wani irin matsewa a qirjinta. Tsakiyarsu ta ajiye tray din coffee din,saidai,ta ware cup biyu kadai. Nanay ta zubawa ta ajiye a gabanta,sannan ta sake zubawa a dayan. Sai data saci kallon akhnan din,sannan ta sanya qaramin tray a qasan mug din. Ta matsa daura dashi tana lanqwashe murya. "Gashi obbo" Ta qarasa fada tana ajiye masa a gabanshi. Hannu yasa ya janyeshi gefe idanunsa na sauka kan fuskar akhnan. "Daukeshi daga kusa da nan.....na nanay is okay" Ya fadiwa saamee ba tare daya kalli fuskarta ba. Ta lumshe idanunta a hankali tana budesu saboda tuni qamshin ya buwayi hancinta da wani irin yanayi me daga hankali. Kaf qamshin nan da yakeyi wani abu na daban yake zame mata yana sake hautsina mata ciki. "Are you okay?" Ya fada muryarsa can qasa da wani irin kulawa. Kai ta daga masa a hankali tana qoqarin qaqaro murmushi,sai ya dora hannunsa a hankali saman bayan hannunta idanunsa cikin nata. Gabanta yayi wani mummunan faduwa. Wani abu ya sauka a hankali yana mamayar zuciyarta. Kulawarsa.....kulawar da yake bata ta tsaye mata a rai da wani irin matsanancin kishi. "Me yasa batason qamshin coffee.....me yasa?" Ta tambayi kanta. Tantancewa takeso tayi,tana son sanin dalili,sai ta dauki wani mug din ta cikashi taf ta tura gabanta. "Ga naki" Ta furta idanunta akan akhnan. Iskar data shaqa ta shiga sosai cikin cikinta,ta soma hautsina mata duk wata nutsuwarta da walwalarta,take ta tattara wani irin amai cikin qasa da second biyar ta soma yunqurin turo mata shi waje. Yunqurin aman da sautinsa ya daga haisam daga mazauninsa cikin qiftawar idanun da baisan zai iya hakan ba sai yanzu. Sai akan akhnan din. *zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 08187255862 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 08187255862 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 144* "Me ya faru?....giiftii....I'm sorry.....sorry please" Shine kalman da yaketa maimaitawa kawai da wani irin rudadden yanayi. Kaman aman na jiransa ne ya isa gabanta,gaba daya ya soma fitowa ba tare da wani jiran komai ba. Kai tsaye ta soma wankeshi tana wanke kyakkyawan jubah din jikinsa. Dukkaninsu hankulansu yayo kanta,nanay ta tashi itama daga mazauninta ta iso gaban akhnan din tana qoqarin riqeta,saidai kuma me abun ya rigata,tuni haisam ya sanyata a jikinsa yana jin yadda jikinta dukka ke girgiza saboda qarfin aman. Damuwarta na yadda zata kauce masa ne kada ta batashi. Tanata qoqarin kauce masa amma sake sakata yakeyi a jikinsa yana tare aman. "Sannu.....I'm sorry" Shine kawai abinda yake fadi. Ya rikice gaba daya saboda ganin yadda farar fuskarta ta soma zama jajaja saboda azabar yunqurin. Matsanancin bugawar da zuciyarta keyi,da tashin da hankalinta yayi na fahimtar abinda akhnan ke dauke dashi yafi komai daga mata hankali sama da irin hukuncin da zata fuskanta daga gareshi. Ta tattara dukkan wadannan yanayin,tashin hankali da bala'e'en kishin da takeji ta cinyesu gaba daya da wani irin yanayi me rad'adi tana takowa zuwa gefansu,tana kuma amfani da dukka wani sign na tashin hankali da takeji tana juyeshi akam dukka damuwa da yanayin akhnan ne. Aareef noorah rumaisa da Aanani dukkaninsu sunyi carko carko daga gefanta. Har zuwa sanda ta kammala aman. Sannu kawai nanay ke jera mata,kamar ta sauke ciwon daga kanta ta dawo dashi mata jikin. Ta kasa tantance cikin biyun wanne zatayi?. Jimamin wahalar da akhnan din tasha yanzu?,ko kuma murnar qara samun tabbatuwar zarginta?. Tana hango fuskar motii ne kawai,yadda zaiji da wannan albishir din. Tanaso ta zama ta farko da zata fara gaya masa wannan kafin kowa ya fadi masa. Idanunta akan haisam,yadda hankalinsa ke a jagule sanda rumaisa ta kawo roba yana gyarawa akhnan jikinta. Matsowa saamee tayi,cikin wannan kulawar da qarqashinta abubuwa ne masu yawa tana miqa hannu zata karba robar da aka kawowa haisam din. "Bari na qarasa mata obbo....kaje ka gyara jikinka". Sau daya tak! Ya daga kai ya aje mata wani irin kallo,take taji dukka 'ya'yan hanjinta sun girgiza. Ta rufawa kanta asiri a hankali ta taka tana ja baya ta basu sararin gurin. Tas ya gyara mata jikinta,ya zare tasa cloak throbe din da ita kadai ta baci ya miqawa rumaisa dukka ya tattara ta fita dasu don bawa hadimai su gyara. Shi ya riqeta da kyau sanda take maida numfashi suna sauka zuwa parlor suna barin dining area din da tuni bayi sun fara aikin tsaftaceshi. Nanay na biye dasu,banda jera mata sannu ba abinda takeyi,har ya zaunar da ita saman sofa,ya tsaya daga gefanta yana ware hannun jubah dinsa daya nade a dazun. "Wata nawa ne?" Nanay dake zaune dab da akhnan din ta fada bayan ta gama qarewa faratanta da tafin hannunta kallo. Dif sukayi ita da haisam din,sai kuma ya juya a hankali yana duban akhnan din. Itama shi take kalla,don bata fahimci komai a maganan nanay ba. Kamar ta tamabayeta,sai kuma haka kawai taji nauyin tambayar nanay din me take tambaya?. "La'ilaha ilallahu muhammadurrasulillahi.....muhammad nace wata nawa ne?,kada dai kacemin bakasan komai akai ba ballantana watanninsa?,yawo kawai kuka dinga yi baka kaita an duba lafiyarta ba?" Nanay ta fada tana tafa hannu sannan ta kama haba idanunta akan haisam din da yayi tsaye ya rasa ma daga inda zai debowa nanay bayanin. Kunyarta da nauyin ta kuma suna sake danneshi,uwa uba kuma shi baisan me yadda akhnan din kanta zata fahimta ba. Idanun nasa ya janye a hankali,ya sake maidawa ga akhnan yana jin wani nauyi yana sake nutsar dashi yana jin nanay naci gaba da mita. "Nace wata nawa ne muhammad?" Ta sake tambayarsa. Kamar ayau an cire mata duk wani shamaki tsakaninta dashi. "Banda sakalci,ka sakata a gaba kuna yawonku abinku,baka damu da sanin lafiyarta ba?. In banda zamani ina ake haka?" Wannan karon dariya ce ta kusa kubucewa daga bakin haisam,saboda gaba daya wadda ake maganar a kanta ma tana zaune tana kallonsu cikin mamaki,kamar ba a kanta ita ake magana ba. Akhnan ta waiga daga nanay zuwa Haisam,sai kuma ta saukar da kanta qasa tunaninta yana kullewa. "Zan sake tambayarka a karo na qarshe" Ta fada fuskarta na nuna serious. Yanzu kam dariyar gaba daya ta mutu a fuskar haisam. Ya zauna sosai cikin kujera. Kamar dalibin da malaminsa ya tsare. "Ban sani ba.....Allah ban sani ba nanay" Yayi maganar yana lumshe idanunsa gami da budesu lokaci guda. Tunda yake bai taba ganin abinda nanay ta yiwa serious haka ba. Fada takeyi da gaske,har sai daya koma a hankali ya zauna. "Nanay" Ya kira sunanta a tausahe. Harara ta balla masa. "Me?" Kaman zaiyi dariya amma ya danne,zaiso yaga yadda zata ganar da akhnan abinda yake tare da ita. "Ba laifi na bane...." "To na waye?" Ta tari numfashinsa hannunta cikin na akhnan din. Ya zare hannunsa daga kan hannuwansu dake harde,ta riqeta sosai kamar wanda ya yiwa akhnan din wani mummunan abu. "Itace...." "Ni?" Akhnan ta tambaya cike da mamaki tana fidda idanu. Me tayi yau haka da haisam ya zabi bayyana laifinta da kuskurenta qarara?. Kaman ba shine ke bata kariya a dukkan muhalli ko gurbi ba?. "Eh ke..taqi yarda.....taqi fahimtar abinda ke faruwa da jikinta". Idanu sosai akhnan ta sake fiddawa,kafin kuma a hankali su koma daidai saboda ruwan hawayen da suka tara na karyewar zuciya. Shuru ya ratsa dakin,kowa da abinda yake kai kawo cikin ransa. A hankali nanay ta sauke kallonta kan akhnan. Ba mamaki bane.....kowacce mace takan tafka nata kalan shirmen da quruciyar yayin cikin fari. Wani abune da kusan yake shammatar kowacce mace,don haka nata kalan shirmen cikin fari kenan. Yadda tayi tsuru tsuru kama me laifi ya sanya nanay kusan sakin murmushi,amma saita maze,ta maida dubanta ga haisam. "Bamu guri.....zamuyi magana" Tsam ya miqe ba tare daya musa ba. Hakan ya masa,qilan tunda nanay ce ta tsaya ta saurara ta kuma fahimta. Shima ta rage masa aiki,amma yadda yasan ta koyi rikici da rigima a kwanakin nan tabbas yau saidai ya shiryawa tarar kowanne rikici nata. Yana sanya qafarsa waje ya tuna abinda saamee tayi dazu,take dan annurin fuskarsa ya bace,ya kuma sauya akalarsa daga sitting room da yayi niyyar zama ya jirasu,ya nufi hanyar dakunan baccinsu. Da farko sanda saqon kiran ya iski saame ta tsorata,ta fara hasashen girman laifin abinda tayi da hukuncinta. Sanannen abu ba,ba wanda zai taso cikin gidan yace baya gane umarni daga gurin yarima haisam,da idanu kawai ba tare da aiki ko magana ba. Ya mata maganan.....amma son gane komai ya sanyata batayi aiki da ita ba,wanda wannan kawai laifi ne me zaman kansa. To amma a hankali sai taji tsoron yana gushewa sanda aka gaya mata shi daya ne,a wani qaramin guri da sukan zauna susha iska. Samun kanta tayi da matsawa ta qara turare,ta sauya hijabin jikinta da mayafi yalwatacce. Ko ba komai.....koda fada zaiyi mata,zataso ya ganta da kyawun nan nata. Duk wani confidence data dauko ya kwaranye sanda ta soma hangen bayansa. Yana tsaye ya bada baya,amma gaba daya kwarjininsa ya cika gurin,kamar yadda qamshinsa ke sauya yanayin gurin da wani irin yanayi me dadin gaske. Ta qarasa bayansa ta tsaya tana sallama kanta a qasa. Kamar baiji ba,sai daya dauki wasu sakanni sannan ya amsa qasa qasa,ya taka ba tare daya waiwayo ba ya isa ga wata kujera dake gabansa kadan ya zauna. Idanunsa ya sauke a kanta a hankali. Karon farko yana jin haushin sonshi da takeyi gaba daya. Besan me yasa ta gaza ganewa ba,baisan me yasa bata fahimci yafi son ya farauci zuciyar da ba ita ta kawo kanta ba. "Saamee" Ya kirata,sunan da muryar suka tsarga mata. "Na'am" "Kinsan hukuncin watsar da umarnin cikin gidan nan....." Ya fada kai tsaye kaman me bata amsar tambayarta bame tambaya ba. "B....ban..." Ta fara yunqurin yin magana. "Banyi tunanin....." Ta sake yunqurin fada amma sai ta kasa qarasawa sanda ta tuna ba'ayi masa qarya. "To ki fara tunani daga yau" Ya furta da wannan nutsuwar tasa da kwarjinin nan dake bugarta. Tadan daga kanta sannan ta sauke,ta san muryar nan. Muryar da haisam ke amfani da ita idan haqurinsa ya qare. "Akwai abu daya da nakeso ki fahimta" Ya fada yana dakatawa. "Kin taso a gidan nan." "Nanay ta raina ki." "An ba ki mutunci." Sai ya tsaya. "Kuma saboda mutuncin nan ne nake magana da ke cikin girmamawa." Zuciyarta taji ta buga da kalmar girmamawar daya ambata. Amma kalmar da ta biyo baya...ita ce ta karya duk wani fata da ya rage mata. "Daga yau." Ya fada a sarari. "Idan ni da matata muna wani wuri..." "Ki bamu guri" "Me yake nufi?" Ta tambayi kanta da wani irin nauyi da tashin hankali daya saukar mata. Kaman yasan abinda take tambayar kanta din yace. "Ina nufin....duk inda muka zauna,kibar wajen". Idanunta ta lumshe tana jin tashin hankali. Ta fahimci abinda yakeyi,yana rufe qofa ne. Don wajibi ne dole ne akan kowa cikin masarautar biyayya ga umarninsa muddin yana son ci gaba da zama. Ya rufe ya kulle mata duka sauran wata qofa da take da fata a kanta. "Kada ki sake shiga tsakanin zamanmu.....kada ki sake kawo wani abu a zamanmu.....kada ki kula da komai daya shafemu a irin wannan zaman...musamman ita,ni zan kula da ita" Hawaye ne suka zubowa saamee masu wani irin dumi. Ba saboda an yi mata ihu ba. Ba saboda an wulaqanta ta ba. A'ah....saboda ta fahimci saqon sosai sama da yadda take tunanin ma zata fahimta din. Ya koreta ta ruwan sanyi daga gurin da take da fata,ya koreta daga rayuwar gidan gaba daya a fakaice. Sai Haisam ya qarasa da kalma daya cikin nutsuwa. Amma mai nauyin da ya isa ya rufe kowace qofa.💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 145* "Ki girmama iyakar da ke tsakanin ki da matata." "Saboda ba zan sake maimaita wannan maganar ba." "In sha Allah" Ta fada muryarta tana rawa,sannan ta juya cikin tashin hankali tana komawa ciki. A wannan karon ta fara zargin kanta. Ta yaya ta bari idanunta suka kulle har take neman zubdawa kanta mutunci da kimarta na diya mace?. Anya wannan hanyar zata bulle mata kuwa?,anya ba zata koma da baya ta maida akalar hankalinta da tunaninta inda ake nemanta ido rufe da dukkan qauna ba?. (Nidai nace oho....nacin soyayya dai bana diya mace bane wadda tasan ciwon kanta). *A K H N A N* "Ciki?...nanay ni?" Ta fada da wani tsoro a muryarta tana fidda idanunta waje tana nuna kanta da yatsanta. Murmushi me qarfi ya qwacewa nanay,ta danyi qasa da kanta tana karantar tsoron cikin sosai daga idanunta. Sake matsowa kusa da ita tayi ta kuma sake kamo hannayenta tana karantar yadda take buqatar a nutsar mata da zuciya da bayanin da zata gamsu. "Eh....ke din". "Amma nanay.....banji ciwo ba" Tayi maganan da yanayin dake nuna sakalcinta a fili. "Duk wanda yake da ciki sai yaji wani ciwo ne na daban?....sannan baki lura da yadda kikejin gajiya ba.....zaben abinci?,rashin son wani qamshi ko wari da sauransu?,duka wannan ba ciwo bane?" Nanay tayi maganan tana duban tsakiyar qwayar idanunta. Shuru akhnan din tayi,wani irin shuru da ya nuna zurfin nazarinta sosai. Murmushi nanay tayi,ta miqa hannu ta shafi gefan fuskar akhnan din a nutse. "Nima na taba zama sabuwar amarya" "Kuma na taba daukar ciki" Ta fada tana murmushi,maganan ta yiwa akhnan nauyi da yawa,tayi qasa da kanta tana jin kamar zata narke. Ashe dai duk yadda ta dauki nanay a matsayin uwa....akwai wani abu da ba lallai ya sauya ba. Surukuta.....bata sauyawa,koda wannan matar zata uwa gareka. "Uwa tana gane wasu abubuwa kafin a gaya mata." "Mijinki....akhnan,akwai wata boyayyar soyayyar da yake miki wadda ni kaina basan da ita ba. Tunda muka zauna a nan idanunsa yana kanki sau ba adadi.....yana kula da dukka motsinki,shi kansa jikinsa ya fara sanin abin da ke tare da ke kafin hankalinsa ya gane." Kunya ta sake narkar da ita,ta sakeyin qasa da kanta sosai. "Akhnan" Nanay ta kira sunanta a tausashe. "Allah ya baki wata ni'ima me girma"Hawayen farin ciki suka fara taruwa a idanun Nanay. "Zaki zama uwa idan Allah yaso" "Ni kuma zan zama kaka" Ta qarasa fadan maganan da wani feeling sosai cikin ranta tana jin kamar ta hadiye akhnan. A wannan karon akhnan ta sauke idanunta kan cikinta. Har yanzu tana jin abun kamar almara,kamar zuciyarta na gaya mata ba zata yarda gaba daya ba. Amma wani abu a zuciyarta ya fara canzawa. A hankali.....A hankali. Kamar tana fara fahimtar cewa rayuwarta ta shiga sabon babi ne. Wani irin farinciki ya mamaye zuciyar haisam dake tsaye a bakin qofa yana kallonsu,yana kallon komai,sai ya sauke hannuwansa qasa a hankali yana jin shima qwalla tana cika masa idanuwa. Baisan girman karamci irin na Allah iya adadinsa ba. Banda shi.....ba wanda zai maka haka. Ya maka baiwa ya sake qara maka da wata. ★★Wani hukunci ta yankewa kanta na koyon komai da komai a sanda duka haisam baya kusa. Cikin awannin da tasan zaije ya dawo. Ta yanke hukuncin zama cikakkiyar matar auren da zata bawa miji kulawa,ta kuma kula da yaran da zata haifa a gaba. Ko kusa ko alama bata bari yasan da wannan shirin ba. A hankali kuma a boye take koyon komai. Saboda a yanzun....ta sani bata da komai....bata da wani abu da zata bawa haisam bayan wannan kulawar,bayan ta iya komai da yakeso yake kuma buqata. Ta sani.....babban kuskure take aikatawa,saboda yadda haisam din idan yana gida koda daukan cup baya barinta tayi,hakanan idan zai fita sai ya tabbatar da dukka hadimanta biyar dinnan dama baba hannatou daya dauko mata ita daga Niamey tana kusa da ita. Tunda take....ko a tarihi bata taba ji ko ganin inda ake lelen ciki irin nata ba. Ta sani tabbas banda tsaurara tsaro akan fitar maganan cikin da haisam ya yanke ya zama abune daya faru cikin sirri saboda sharrin ido da baki.....tayi imani da yanzun haka anacan ana shagali na kwana da kwanaki akan cikin. Don gaba daya sunyo kabbara akansa. Tsakanin nanay motii dasu oga Anaani batasan waye yafi qaunar wannan d'an tayin dake kwance a mararta ba. A cire ta oga kwata kwata haisam.....nashi abun baya da misali dana kowa a cikin su,don tabbas inda yana da hali,daidai da numfashi ma cewa zaiyi zaiyi mata shi. Batasan tana da kunya har haka ba.....sai sanda morsa safiyya ta kirata tana mata sannu da jiki. A maganganun morsa safiyya ta tabbatar nanay ba zata iya boye wannan farincikin ba....ba zata iya qin gayawa 'yar uwarta ba. Sanda sultane ya kirata zai mata sannu da jiki a wani lokaci da jikinta yayi weak,haisam ya dage lallai sai an saka mata drip saboda tafijin qwarin jikinta,kashe wayar tayi. Kunya ta dinga ji,ba zata iya magana da sultane ba,bayan ya fita sanin komai da akayi aka samu cikin. Ta dora idanunta akan haisam dake zaune a gefanta yana yanka mata fruit,sai ya dage mata girarsa dukka biyun,daya daga cikin alamun tsokanarsa kenan idan yaso. "Bakaji kunya ba?" Ta tambaya da muryarta da tayi laushi saboda wahalar da tasha jiya. "Name?" Ya fadi yana kashe mata ido daya. "Haisammm mana" Ta fada a karye. "Wash Allah na" Ya fadi shima yana lumshe idanunsa gami da dora tafin hannunsa a qirjinsa. "Har yau.....ba abinda ya canza....har yau ina bala'in son naji sunana abakinki" Yana sauke maganan yana jifansa da pillow. Saurin fushinta ya motsa,wani abu ya tsaye mata a wuya. Haisam ya rainata,ta lura kallon yarinya qarama cancan yake mata. Idan tana magana serious shikam bai taba bata muhimmanci ba. "Bakajin kunyar bappi na.....kasan me kayimin na samu ciki,amma har zaka iya gaya masa ina da cikin?" Ta fada hawaye na silmiyo mata. Dariya taso qwace masa,amma yasan bai isa yinta a wannan lokacin ba. Maganan gaskiya ya rasa wanne kalan sakalci yake damun akhnan din. Ita ba 'yar fari ba....ita ba auta ba. Duk da wani bangaren ana iya kiranta da auta din,tunda itace ta qarshe a wajen mamminta. Komai ya ajiye ya isa inda take,ya tsugunna saman qafafunsa yahau aikin lallashi da share mata hawaye. Saboda ya sani......indai nanay tazo ta samesu a hakan....bame qwatarsa sai Allah. Laifin duniya duka nasa ne. Nanay.....ba wai tana son akhnan bane kawai. A'a....yanzu tana kallonta ne da idanun uwa.....suruka....kuma mahaifiyar babban jikanta na farko. Akhnan ta fara jin kamar Nanay tana zaune ne a gidansu,saboda kullum sai ta kira. Safe.....rana....dare. "Kinci abinci?" "Me kika ci?" "Me yake damunki?" "Me kikeso yanzu?" "Ina fata haisam bai takuraki ba" "Akwai abinda kike buqata?" "Me kikeyi yanzu?" "Qarfe nawa kikayi bacci?" "Basu katse miki bacci ba ko?" Wadannan tambayoyin dama tarin wasu ya sanya haisam ke kame kansa kafin sunanshi ya shigo list na 'yan tuhuma. Shi kansa bai tsira ba,wani lokaci shi take kira ba akhnan ba. Akwai randa yayi wani mistake ranar ya gane a yanzun baida wata faada a gurin nanay. Akhnan da abinda ke cikinta sun karbe gurbin. "Muhammad" Yana tsaka da aiki a sannan a office dinsa dake jimma. "Na'am nanay" "Taci?" "Me taci?" Ya tambaya saboda kanshi ya buga da tarin gyare gyare da sukeyi a kamfani,da kuma settling ayyukan akhnan na sahel couture dana maison akhnan daya hadawa kansa gaba daya. "Dama na sani....baka tambayeta ba....anya muhammad kana kula da ita yadda ya dace kuwa?" "Nanay...." Ya kirata don bada uzuri amma ta katseshi. "Ka kirani idan ka isa gida" Sai ta katse wayar abinta. "...I failed an inspection." Ya fadi a fili yana dafe kanshi. Bayan kwana biyu kuma sai ga motoci sun iso gidan cike da kayan abinci. Fresh fruits,honey da traditional foods da yawanci masu juna biyu suke ci. Komai carefully selected,kana kalla kasan da takatsantsan aka shirya komai. Da kanta ta sauko ta duba cartons din cikin mamaki. "Waye ya turo wannan?" Birra tayi murmushi tana dubanta. "Nanay." Sai Akhnan ta dafe goshinta tana dariya. Jiya suka gama wannan case din da haisam. Yanata complain. Duk kulawar da yake bata shi ya lura ma kamar nanay ta rainata. Kamar ma baya yin komai,yau ga aiken kayan abinci da fruit bayan duka stores dinsu na gidan ba wanda ba ajiyayyen kayan abincin da zai shekara biyu su da dukka hadiman gidan suna amfani dashi komai yawansu. "Allah ya barmin nanay na" Ta fada tana murmushi,ta sake matsawa tana kuma buda kwalayen. Har ma da notes,small notes a takaddan da handwriting din nanay dake nuna rubutunta ne. "Ki ci wannan da safe." "Kar ki bari yunwa ta same ki." "Ki huta sosai.". Saita dauki takardar a hannunta tana komawa ciki da ita.💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 146* ★Da wani yammaci.....daya daga cikin yammacin da haisam yake addis ababa. Yaje can headquarter dinsu zaiyi supervision na wani aiki da aka tura wasu daga nan office dinsu under na'urorin da suke communicating. Yawanci idan zaije addis ababa din ta private jet yake tafiya ya kuma dawo,baya ma shiga kuma sai idan wani abu ya taso,don haka duka duka awanni uku zuwa hudu yakeyi. Yaso yaje da akhnan din.....amma baisan ya akayi yayi subutar baki yana sallama da nanay din tace kul kada ya soma daukar mata diya,shi din dai sai ya dawo. Hakanan ya haqura din,amma duk bayan wasu mintuna sai taga kiranshi ko tex dinsa. Tashinta a bacci kenan da yammacin,tayi sallah ta sake watsa ruwa saboda yanzun wani irin jin zafi ne da ita. Ta shirya cikin wata cotton gown data sauke har qasa ta rufe mata qafafunta. Wani material ne olive green me taushi da rashin nauyi. Ta kame gashinta da wani band,hakan ya bawa gashin nata daman sauka a gadon bayan ta yana lilo. Dan matashin cikinta daya soma bayyana tun a wata uku ya dago rigar kadan. Tayi wani irin kyau irin na masu farkon shigar ciki. Ta sauko downstairs da wayarta a hannu tana murmushi bayan ta gama duba saqon haisam. "Giiftii.....my princess.....bana gane aikin nan sam....anya bazan musu shirme ba?,the silent one bazai samu suspension ba kuwa?,nanay taqi fahimta.....ke aljihuna ce....na gaba gaba" Maganan ya sakata dariya da nishadi sosai,da wannan a fuskarta ta qarasa saukowa. Buhaina da bushira ne kawai a parlour din,suna turareshi da sassanyan qamshin nan na shuwa incense and more,daya daga cikin qamshin da har yanzu bata daina so ba.....basa damunta kuma (+234 704 229 3387 tasted and trusted,zaki godemin sosai). Da girmamawar nan da qauna dake tsakaninsu da uwar dakin nasu suke mata barka da saukowa. Ta amsa musu itama da kulawa. A ranta tana jin kamar lokaci yayi da suma ya dace ta aurar dasu,koda kuwa zasuci gaba da rayuwa da ita ne. "Nanay tazo" Buhaina ta fada da murmushi,don suna matuqar son zuwan matar gidan. Badai mutunci da karamci ba. Da dan mamaki ta daga idanunta daga amsar da take kan bawa haisam din idanunta a waje. "Yaushe?,tana ina?" "Yanzu ne,bata jima na,tana kitchen" "Kitchen kuma?" Ta tambaya da mamaki,sai kawai ta fara takawa da kanta zuwa kitchen din ba tare data jirasu ba. Tun daga nesa ta hangota cikin cook ma gidan tana duba abinda ake dafawa. "Me yasa suka saka spice haka?" Ta fadi tana d'an d'ana wani fried chicken da suka kammala. Cook din ta tsaya cak tana rusunawa. "Ban dauka ba'a buqatarsa ba ranki ya dade" Kai nanay ta girgiza "Kunsan ba ita kadai bace.....ba za ku dafa kamar yadda kuka saba ba,a daina using nashi kwata kwata,yayi strong da yawa" Ta qarasa maganan cikin jikinta kamar tana jin isowar akhnan ta maida idanunta can. Ajiye abun hannunta tayi ta tako tana marabtar akhnan din. Cikin kunya ta zame mata shirin gaidata amma saita rungumeta tana tambayar lafiyarta. Tare suka baro kitchen din,nanay na mata tambayoyi game da lafiyarta. Sai data duba komai nata,tare suka zauna zaman cin abinci,wanda sai da suka zauna din sannan taji qarar da wayarta takeyi. Koda ta duba haisam ne. Ya tara mata messages da miscal saboda jinta shuru suna tsaka da magana,sai kawai tabi kiran. Bugu daya ya dauka kaman daman jiran kiran yake daga gareta. "I can't wait my princess,on my way,nan da fifty minutes zan qaraso" Tadan fidda idanunta tana mamaki,kafin ta sauke wayar sanda ta jishi ya yanke kiran. Ga mamakinta,adadin wadannan mintunan su ya dauka taji shigowarsa shida guard dinsa. Ta lumshe ido a hankali sannan ta bude tana jin kamar wani sashe na jikinta ke dawowa gareta. Sanda ya shigo nanay ta tayar da sallah bata parlor din. Ya bude hannayensa yana dubanta gami da jiran isowarta jikinsa kamar yadda suka saba. Sai ta noqe kafada,wannan ya sanyashi jefo qafafunsa da sassarfa yana fadin. "Ba lokaci my princess......bazan iya jiran wannan jan ajin naki ba yau" Ya qaraso kusa da ita ya sanya dukka hannayensa yana shirin dagata "Nanay" Ta fada da sauri tana zaro idanu waje,daidai sanda nanay din ke fitowa,sai yaja da baya yana shafa sassalkar sumarsa idanunsa a qasa. Da wannan dabi'artata ta ta gani amma kaman bata gani ba ta zauna. Ya zauna qasanta yana gaidata cike da kulawa. Su danyi hira kadan kafin ya miqe yana duban akhnan din. "Ku jirani na fito sai muci abincin tare nanay idan ba damuwa" Ya fada idanunsa akan akhnan. "Na kusa tafiya....amma idan baka zauna ba zaka sameni" Ta fadi tana duban agogon hannunta. "Okay.....yanzun in sha Allah" Ya fadi idanunsa da fatansa dukka akan akhnan. So yake ta taso.....so yake ta biyoshi. Yanason yaji dumin jikinta,yana so ya aza hannunsa saman cikinta yaji tudin ajiyarsa. Yanaso ya shanshanata,ya shanshana qamshin nan nata. Yayi missing nata ba dan kadan ba.....yayi kewarta kaman ya dauki wasu kwanaki ba tare da ita ba. Amma har ya soma takawa zuwa ciki akhnan batayi niyyar wannan ba. Koda ya shiga dakin sai ya kasa komai,ya cire socks dinsa da cufflinks dinsa,amma duka sai ya jefar. Yaji sam bashi da wani energy. Ya tako a hankali yana komawa bakin qofar dakin ya bude a hankali ya tsaya ta inda zai iya ganinta. Hankalinta kwance a gaban nanay,ya saki qofar ya koma da baya yana sauke numfashi. Daga ita har nanay kaman suna mantawa dashi idan suna tare,ya rasa wanne irin wariyar launin fata suke masa haka. Sake takawa yayi ya koma bakin qofar,wannan karon kai tsaye ya kirata. "Akhnan" "Na'am" Ta amsa tana waiwayowa,suka hada idanu amma sai ta basar. Duk da tana jin kewarsa itama,duk da tanason zuwa gareshi,amma kunyar nanay takeji "Ina kika ajiyemin kayan nan da na bari a gefan bedside" Da farko ta shiga tunanin wadanne kaya?,amma daga bisani data dago maganan da kuma yadda ya zuba mata ido sai dariya ta kusa zuwar mata. "Suna inda ka ajiye....." "Giiftii" Nanay ta kira sunanta. "Na'am" "Tashi kije gurin mijinki" Ta fada a nutse don ta fahimci komai ita. Sai data dan dakata kadan,sannan ta miqe a kunyace tana takawa zuwa dakin. "Ki kula da kanki" Nanay ta fada a hankali,kalmar data saka akhnan ta kusa nutsewa a gurin. Tasan yana kusa....amma bata dauka yana kusa da qofa haka ba,sai ji tayi ya jawota a tausashe cikin jikinsa. Juyo da ita yayi suna fuskantar juna,idanunsa sunyi wani irin laushi cakude da gajiya da wani irin shauqinta da kewarta. Ya motsa labbansa a hankali da zummar yin magana.....amma saita hana masa wannan damar ta hanyar hade bakunansu guri daya. Wani irin fitinannen kiss take ajiye masa wanda ya qarasa cakuda hankalinsa gaba daya,ya sake ingizashi wata duniya data sanya ya gaza komai,har sai daya dauketa cancankat dinta ya maidata saman bed din. Zazzafar maraba ya samu da wata irin tarba ta musamman data sanyashi jin kamar sannan komai yake wakana bayan kammaluwar lamarin. Baisan kowacce mace a duniya ba sai ita....a kanta ya fara sanin me ake kira da wannan abun....amma shi kansa ya tabbatar yayi imani ita din ta musamman ce. Ya sani ba shakka samun irinta cikin mata kadanne. Tasa hannu kaman zata tsone masa idanu saboda yadda yake faman qare mata wani narkakken kallo sanda kawunansu ke saman pillow daya suna huce gajiya. "Nanay tayi kuskuren fahimta......ina jinta tana cewa ki kula da kanki.....batasan yaronta ba,Allah sarki,yanzu ya zama salihi......diyarta ita ce fitinanniyar" Yadda yayi maganan dole ya bata dariya. Ta cusa kanta cikin pillow tana qyalqyalawa. Ita kanta da farko abun yayita bata tsoro,har ta kaita ga yin binciken dalilan dake sawa buqatar mace ta qaru. A cikin jerin sawun taga harda pregnancy saboda sauyawar hormones,hauhawar wasu daga ciki. "Shikenan.....yallabai yarimana ayi haquri,yanzu dai kada na takurawa ya sheikh,ya kamata na tafi hutu koda na sati biyu ne....." "Wallahi baki isa ba...." Ya furta yana cafkota sanda take qoqarin sauka daga gadon ba tare daya bari ta gama furta abinda zata fadi ba. Dariya sosai ta saki,saboda yadda yayi wata sufa yana kamota. Sai shima daga baya abun ya sanyashi sakin tattausan murmushi me qaramin sauti. "Wannan tsarin shine daidai na.....ta yaya zakimin qauro?" Ya fada yana matseta cikin jikinsa. *_BAYAN WATA BIYAR_*💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 147* Sannu a hankali kwanaki ke juyawa suka bada wadannan watannin. Watannin da suka maida cikin akhnan ya zamana wata takwas daidai da wasu 'yan kwanaki. Cikin 'yan biyu ne kaman yadda scanning ya nuna musu,amma yayi wani irin girma daya sanya haisam ya sake maidawa gami da tattara dukka hankalinsa a kanta. Komai kusan da wahala yake zuwa mata.....amma duk da wannan wahalar abubuwan sai suke juye mata da sauqi saboda kasancewar jajirtaccen namiji a gefanta. Uwa uba kuma taimakon amintattunta irinsu birra,wanda numfashi ne kawai basu da ikon suyi mata,amma komai da take buqata saidai idan bata nuna hakan ba. Yayin da cikin ke qara girma wata bayan wata,cikin zuciyar Haisam ma wani abu ke sake canzawa. Ba soyayyarsa ga Akhnan ce kawai ke qaruwa ba......Aah,wani irin girmamawa yake mata ta musamman. Tattalinta da tattalin dukka al'amuranta. Musamman da aka wayi gari akhnan din ta zama cikakkiyar mace a gareshi. Bata damu da nauyin da take dauke dashi ba......bata damu da irin matsayin da Allah ya bata ba. Bata kuma damu da gidan data fito ba.....shi MUHAMMAD HAISAM shi dinne kawai a gabanta. Ta yaya zata faranta masa?. Ta yaya zata kula dashi?. Musamman data fara fahimtar irin yawan matan da zuciyoyinsu ke yawo a kansa. Yawan matan da burinsu a ko yaushe shine yadda zasu mallakeshi da komai nasa. Tun daga rainon cikin ta sake jin wata sabuwar soyayya da qaunar mahaifiyarta. Tun a sannan ta sake ganin kimar morsa safiyya....nanay....dama duk wata uwa da zata bude ido ta ganta rungume da yaronta. Ta shiga wani sabon yanayi gaba daya. Wasu kwanaki tana cike da kuzari. Wasu kwanaki kuma tana gajiya da qananun lalure lalure. Amma duk da hakan,ta zabi ta zama jarumar uwa. Ta zabi ta zama jajirtacciyar mata me tsananin kulawa da mijinta da komai daya shafeshi. A irin wadannan lokutan haisam ya koyi abu guda daya. Biye mata da kuma lallashinta cikin kowanne yanayi. Ta zama wata mafadaciya me saurin fushin da babu dalili,takan iya sanya masa kuka haka siddan ba tare da yasan yayi komai ba. Duk lokacin da ta ce "Ban san me yasa nake kuka ba." Sai kawai ya jawota jikinsa. "To ki yi kukanki.....yi kukanki yadda zaiyi miki" "Ba ma san dalili ba fa." Takan maimaita fada wani lokaci cike da tsoron kanta da kanta na yadda komai da komai da yadda yanayinta yake sauyawa. "Ba lallai sai kin sani ba." Zai sake amsa mata da kulawa a tausashe. Hakanan sai ya zauna yana lallashinta,tsadaddun lokutansa duka ya sarayar mata har sai ta gama. A gefe guda kuma duk wasu harkokinsu basu fasa garawa ba. Kamfanonin su na ci gaba da bunqasa.....kasuwancin na wani irin habaka daya bawa haisam mamaki cikin watannin. Sau daya ya taba jin wani yana fadin,wani lokaci wani arziqin silar aure Allah yake sake bude maka shi. Baisan adadin abinda ke shiga account dinsa ba kullum rana. Sabbin yarjejeniyoyi na shiga. Sabbin cinikayya na budewa. Sau tari ana iya samun Haisam a babban conference room yana tattaunawa da manyan shugabanni. Yana yanke shawarar da zata iya motsa miliyoyin daloli. Amma a tsakiyar meeting wayarsa zata yi haske,message daga giiftii dinsa zai shigo. Ko yaya ya fita suna tare akan waya. Tun tana cewa ya maida hankalinsa kan ayyukansa idan ya fita harma ta daina ta biye masa. Haka kawai tsakiyar meeting yana iya daukan break,kowa sai ya jira,yakan shiga rest room ya zauna ya kira takanas don yaji muryarta da lafiyan yaranshi. Yaran da tun kafin suzo duniya batasan irin soyayya da mutane da dama ke gwada musu ba. Duk muhimmancin meeting idanunsa basa gaza sauka kan message dinta. Murmushi yakan bayyana a gefen lips dinsa. Abin da ma'aikatansa suka daina mamaki da gani,wannan murmushin da idan ka ganshi saman fuskarsa to tabbas yana da alaqa da princess dinsa. Su kansu yanzu sun sani......CEO dinsu ya zama mutum daban idan maganar matarsa ta shiga. Sannu a hankali akhnan ta fara shiga wasu daga cikin ayyukan kamfanoninsu daga gida. Ba wani dogon stress ko aiki me wahala ba. Saboda Haisam ya hana ta wahala sam sam. Tana bibiyar reports,tana ba da ra'ayinta akan abubuwan da suka shafi gudanarwa,tana shiga online meetings idan tana da kuzari. Da wani yammaci suna zaune a library na gidansu. Takardu ne a gaban haisam,akhnan kuma laptop. Yayi nisa qwarai cikin lissafin ribar da sahel couture ke kawowa,wata irin riba me ban mamaki cikin watanni kadan da ci gaba da gudanar da kamfanin wanda akhnan ke jagoranta daga gida. Da tare suke aikin,sai yace ya bata break,ta zauna tayi relax kawai na wasu mintuna. Sai data huta sannan ya kalleta. "Time up" Ya fadi yana dubanta,sai ta dage girarta tana murmushi. Sai da yaga taci gaba sannan ya maida hankalinsa ga takardun da yake lissafin. Haka kawai cikin jikinsa yakejin idanunta,sai ya dago kai a nutse yana dubanta. Tarar da ita yayi ba ta aikin,ba kuma karatu takeyi ba. Bata komai,kawai ta tattara dukka idanunta da nutsuwarta a kansa,kallonsa kawai take yi,zara zaran eyelashes dinsa dake motsawa a hankali saman takardun suna sake sanyawa tanaji yana sake burgeta. "Me?" Ya tambaya a hankali. "Nothing." Ta fadi murmushi yana subuce mata a hankali "Akhnan." Ya kirata da sautin dake nuni da kada ki sake kiyimin qarya. "Ina tunanin..." Ta yi murmushi. "...yadda yaranmu zasu yi." Sai ya tsaya cak,takardun da ke hannunsa suka rasa muhimmanci na dan lokaci. Ajjiyesu yayi a hankali yana fuskantar inda maganarta ta dosa. "Akhnan" Ya sake kiranta a tausashe. "Kina tunanin......inda za'a bani zabin qwace komai dana mallaka.....a barmin ke da yaran da zaki haifamin.....bazan zabi zama matalauci daya mallaki kyakkyawar gimbiya da yaran da suka haifa ba?" Maganan ta sauka a zuciyarta da kunnenta da wani irin laushi daya tilasta mata lumshe idanunta gami da budesu. "Naji tsoro....." Ya bude idanunsa duka yana dubanta. "Naji tsoro sanda na fahimci zuciyata ta fara sonka a sanda kai ko kallo ban isheka ba. Naji tsoro sanda na fahimci na fada tarkon qaunarka. Naji tsoron rasa kimata.....darajata da martabata. Ashe abinda ban sani ba,wannan soyayyar....wannan son shine silar da zai fidda rayuwata daga duhu zuwa haske.....wannan son shine zai mallaka min LU'U LU'UN dake gabana.....LU'U LU'UN da nake shirin tattakeshi da qafata ba tare dana gane shi bane". Ta cikin idanunta kadai ya fahimci dukkanin gaskiyarta. Ta cikin idanunta kawai ya fahimci gaskiyarta kenan take fada daga zuciyarta. Sai kawai ya ture kujerarsa baya,ya miqe a hankali yana takowa. Idanu ta fidda kadan murmushi yana subuce mata. "Me?,ina zaka?" Ta tambaya tana sake fidda blue eyes dinnan nata da suka sake girma. "I've missed your warmth..." Ya furta a hankali yayin da ya yi mata rumfa da hannayensa a saman kujerar da take zaune. Idanunsa suka sauka kan nata da wani irin yanayi me sanyi. "Let me stay here for a moment." Ya fada sanda yake mata rumfa saman kujerar da take zaune akai. "Haisammm" Ta fada da wannan yanayin da yakeso. "Akhnan" Shima ya furta da wata sirrintacciyar murya yana sake hade tazarar dake tsakaninsu. "Aikin....." Bai bari ta qarasa ba,ya toshe mata bakinta da nasa. ★Watanni sun yi nisa. Cikin Akhnan ya kai girman da ko juyawa a bacci sai ta yi tunani kafin ta motsa. Wani yanayin da ita kanta yake bata tsoro,saidai tana dannewa ne kawai saboda yadda hankalin haisam gaba daya ya tattara a kanta. Karfe biyu na dare,gidan gaba daya ya yi shiru. Wani irin shuru me nutsuwa. Ba abinda kake ji sai sautin motsin security da suke kwana aikinsu cikin gidan kafin safiya wasu su canjesu. A hankali ta farka. Wani irin yunwa ce ta tashe ta daga baccin daya dauketa tun dazu,batasan ma ya akayi haisam ya maidota daki ba. Wani irin nauyin bacci takeyi,ta kwanta da wayarta a hannu tana lissafa EDD dinta. Sati shida ne ya mata saura a yadda scanning da calendar yake nuna mata. Ta yunqura tayi qoqarin tashi ba tare da ta tashi haisam ba. A hankali ta zame daga jikinsa,bataso ta farkar dashi,bataso ta hanashi baccinsa,saboda yini yake yana ayyuka biyu. Tata hidimar,da kuma hidimar kamfani. Duk da wani lokaci yana rikida ya koma dan binciken sirri boyayyen aikinsa da duniya batasan dashi ba. Saidai amma kafin qafarta ta taba qasa,muryarsa ta fito daga dim light din dakin. "Ina za ki?" Tadan firgita kadan,saboda yadda tayi takatsantsan gurin tashi batayi zaton zai ji barinta jikinsa haka da wuri ba. Ta yi rolling eyes dinta tana sauke numfashi a hankali. "Ina jin yunwa." Maganan ta sanya ya bude idanunsa gaba daya a hankali. Sai yaji kaman shine sila. A dazun sai data tabbatar ta gama kaishi duniyar da yakeso kafin su koma parlor inda a nan bacci ya dauketa,sai shine ya dauketa cancakat ita da cikin,yana takawa da takatsantsan saboda yadda ta ninka nauyinta. Sai a sannan ya sake kallonta da kyau,tausayinta yana ratsashi a hankali. Cikin bai mata muni ba.....amma kuma komai na halittarta ya canza. Ya sani,tana jin jiki koda bata fada ba,tsabar juriya ce irin tata da bai taba zata tana da ita ba,musamman idan ya tuna first night dinsu,sai gashi tana shirin bashi mamaki. Wannan ya sanya yayi booking medical team qasa uku,duk inda ta fada kota kama zasuje. Bai gaya mata Cs bane,saboda bayaso hankalinta ya daga kafin lokacin. Baya so hankalinta ya tashi ko kadan,ko a jiya da sukayi waya da likitocin yana jiran date ne kawai na randa zasu cire mata cikin. Yanaso ya ganta ta huta hakanan,yanaso ta koma akhnan dinnan daya sani.💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 148* Bude idanunsa yayi gaba daya a wannan karon. "Yanzu kika fara jin yunwar?" "Eh." Ta amsa masa a shagwabe. "Karfe biyu na dare,me yasa baki tasheni ba?" Ya fada yana miqewa zaune sanye da fari qal din wandon pyjamas "Ni ba agogo ya tashe ni ba." Ta fada tana narai narai da idanu ta cikin hasken fitilar daya kunna ta gefan gado. Sai ya yi dariya kadan,ya kama kumatunta ya danja a tausashe "Me kike so acici?" Ya tambayeta "Ban sani ba." Ta fada qwallar nason gangaro mata. "Wonderful." Ya fadi yana sanya yatsansa ya dauke mata qwallar kafin takai ga zubowa. Lips dinsa ya dora saman goshinta,yayi kissing nata softly,sai yaci gaba da barin lips din nasa saman nan yana sauke mata lallausan numfashinsa a nutse saman goshinta. Wani irin nutsuwa hakan ya saukar mata,bai janye ba sai daya tabbatar zuciyarta ta sassauta. "I'm sorry.....kiyi haquri,Allah yana tare dake,kowacce rana qwaya daya tal tarin lada kike samu,double lada saboda yara biyu ne a jikinki.....ke din 'yar aljanna ce in sha Allah". Maganan ya sake sanyawa zuciyarta tayi wani irin taushi,ya miqe ya kama hannunta a nutse yana sauko da ita daga saman gadon. Minti goma bayan haka,akhnan na zaune a kitchen island. Blanket ne a kafadunta wanda haisam ya lulluba mata don taji dadin zaman,da kuma sanyi sanyin daren da akayi ruwa a cikinsa dake ratso kitchen din. Haisam kuwa,wanda manyan kamfanoni ke jiransa safe,yana tsaye yana binciken fridge. Kai ba zaka ce shine wannan zakin ba.....wannan malamin.....wannan attajirin.....wannan yariman da number dinsa ke kadawa cikin manyan diyan jinin sarauta da duniya ke alfahari dasu. "Fruit?" Ya waiwayo yana tambayarta gami da d'age girarsa sama. "A'a." Ta fadi da shagwaba tana bubbuga qafafunta a qasa. Sai ya maida kansa ga fridge din yana ci gaba da bincikawa. Sake waiwayowa yayi yana dubanta da fararen idanunsa. "Yogurt?" "A'a." Ta sake amsa masa tana maqale kafadarta. "Soup?" Ya sake tambaya bayan ya sake bincikawa. "A'a." "Akhnan." Ya fada yana miqewa tsaye daga tsugunnon da yayi yana waiwayowa dukka gareta. Dariya ta fara yi,wata boyayyar dariyar da haisam yake iya ganeta nan da nan duk da boyetan da take qoqarin yi. "Ban sani ba ne." Ta fada tana langabar da kai cikin yin kalar abun tausayi. "Two babies woke me up for this." Ya fada da muryar tausayi shima,sai ya ci gaba da bincike cikin fridge din. A qarshe ya fahimci ta shirya wahalar dashi ne,don haka bai sake tambaya ba ya shiga hada mata wasu abubuwa. "Bismillah" Ya fada yana dora mata saman island din,sannan yaja kujera ya zauna opposite nata. Yatsina fuska kadan tayi,ta saka spoon cikin bowl din. Ta saka na farko a bakinta,ta tauna,sai ta tsaya. "Hmm." Ya daga kansa yana dubanta sosai. "What?" "This." Ta nuna plate din. "This is exactly what I wanted." Sai ya tsaya kawai yana kallonta. "You just said you didn't know what you wanted." "Ban sani ba sai da na gani." Ta fada tana sake kai loma bakinta hankali kwance tana lumshe idanunta. Ya kalli ceiling kamar yana neman taimakon Allah. Sai wata irin dariya ta subuce mata,ta dara sosai har fararen jerarrun haqoranta suna fitowa reras. Kai kawai ya girgiza,yaci gaba da kallonta tana cin abinta hankali kwance har ta kammala. Ta gyara zamanta sosai cikin dabara kaman yadda ta saba tana kallonsa. "Sorry." Ta fada tana kama kunnuwanta. "For what?" Ya tambaya yana dage dukka girarsa biyun. "For waking you." Sai ya kalleta,sannan ya sauke idanunsa kan cikinta. "If you wake me ten times a night..." Ya tsaya da wannan nutsuwar tasa. "...and it means you and my children are okay..." Ya girgiza kai "I'll get up all ten times." Shuru tayi,zuciyarta na narkewa,sai ya matsa kusa da ita,ya gyara mata blanket din da ke kafadarta. "Now finish that." "Na koshi." "Akhnan." Ya kirata da wannan yanayin me nauyi. "Haisam." Itama ta kirashi,kamar kowannensu iyayensa sun saka musu wannan sunan ne saboda dan uwansa. Ba gurin wanda suke jin dadin sunayen sai a bakin daya daga cikinsu. "One more bite." Ya fada yana daga yatsansa guda daya Sai ta yi dariya. Saboda yanzu ta gane wani abu. Tun da cikin ya girma......ba nanay kadai suke takurawa ba....haisam ma ya shiga qungiyar kula da ita da cikakken lokacinsa. Tana motsawa saqo yana shigowa wayarta,haisam yabi wayar da kallo sanda take dauka. Kaman zai hanata sai kuma ya qyaleya,taci abinci,yanzun nan idan 'yan rigimar suka motsa saita narke masa hannun agogo ya koma baya. Idanunta dukka ta fidda waje tana kallon haisam bayan ta janye idanunta daga kan wayar. Tana jin kamar tayi ihu ne,amma kuma tasan dare ne. "Falaak my prince.....falaak ta sauka......ta samu baby girl.....maleek ya zama daddy before you" Ba haihuwar bace ta burgeshi. Yadda take maganan idanunta da suka sake girma da haske a waje. Yadda excitement dinta ya nuna,sai yaji kawai yana dokin zuwan ranar da zata riqe nata babies din. "Next week sunan falaak.....next week bikin shehnaz......aisa....rumaisa da Aanani. Yaa muhammad.....ya ahmad......the whole next week is for us". Shikam kallonta yake kawai yana zaune,ya nannade hannunsa a qirjinsa. Mamakinta kawai yake,bata ko jin nauyin abinda ke jikinta take tunanin bukukuwa da suna. Yana jinta tun jiya take lissafa events events,wanda bayajin ko daya zai barta. Bazaima yarda da zamanta ciki wannan hayaniyar bikin ba sam sam. "Come,let's go to bed my princess" Sai taji ya dagata cak tana tsaka da surutunta. "Malamina.." Ta kirashi da sunan da take kiransa a wasu lokutan. "Sleep babe" Ya fada muryarsa can qasa. "Na sani.....amma banji kace komai ba" "Sai da safe" Ya fada da yanayin daya tabbatar mata bacci yakeso tayi. Bata musu dashi,bata iyawa sam,sai bata sake cewa komai ba,ta maida idanunta ta kulle,har bacci yayi awon gaba da ita. Sanda yaji tai relax sosai ya tabbatar masa bacci ne,sai ya zare jikinsa a hankali ya dauki wayarsa yana sauka zuwa parlor din qasa. Dr farrah ya fara contacting,yasan yanzu haka tana asibitinta,ma'abociyar night duty ce,yasan zai wahala ace tayi bacci a sannan. Sun jima sosai suna tattaunawa da ita,tayi connecting kiran da sauran teams din. A qarshe suka yanke shawarar ajiye kwanaki goma a gaba don cirewa akhnan jariran,don dukkaninsu girma da nauyin cikin yana basu mamaki,suna zuba ido suga wanne irin manyan babies haka zata haifa?. Dalilin da ya sake jan hankalinsu kenan ma wajen cire yaran,kada garin bata dama ya zame mata matsala. Washegari kallonta kawai yake,yana jin kamar ya mata wani kuskure ko ba daidai ba. Itakam shirye shiryenta kawai takeyi. Yana jinsu sanda rumaisa tazo gurinta wadda surukuta takeyi yanzu kawai da akhnan din,duk da girma suke bawa juna sosai,saboda kowacce tana matsayin mata ga yayan daya. ★★★ *_AGADEZ & ETHIOPIA_* Wani gagarumin shirin bikin aure ne ke motsawa tsakanin qasashen guda biyu. Bikin auren da tuntuni sati biyu kafin zuwan lokacin hotuna da short short videos na kayan auren kowacce ya karade social media. Harma wadanda ba 'yan qasashen ba suna tambayar yaushe ne bikin?,'yan wacce qasa ce da sauran su. A yadda aka tsara....za'a faro bikin daga agadez dinne. Za'a dauro auren shehnaz da aisa,sai a daukosu a taho dasu jimma,sannan a nan a daura auren rumaisa da Anani,su karbi su shehnaz.....a basu su rumaisa da Anaani kuma. Saukar safe prince sheikh muhammad haisam aba jifar da gimbiyarsa khadeeja sultane muhammad hammud sukayi a private jet dinsu cikin filin sauka da tashin jiragen sama dake agadez. Kai tsaye kuma motocin alfarma,cikin royal convoy dinnan nasa masu daukan hankali suka daukesu daga airport din zuwa personal home dinshi. Narke masa idanu akhnan tayi,rabonta da agadez tunda aka kammala case din mammina. Ta qagauta taga babyn falaak,ta qagauta taga sultane....ahmad....morsa safiyya da yanzun take kallonta kamar mamminta,da wasu kamannin mammin nata da sai yanzu take ganinsu tattare da morsa din. "Na dauka masarauta zamu wuce" Ta fada tana dubansa,don tun kafin motar ta fita daga airport ma,zuciyarta tana can. Amma lokacin da ta lura convoy din ya kama hanyar personal residence din haisam...sai taji ta kasa shuru. Bai ma dago daga tablet din hannunsa ba ya amsa kai tsaye a taqaice "A'a." Sai ta hade gira. "A'a?" Ta maimaita. Sai a sannan ya dago idanunsa gare ta. "Kin yi tafiyar sa'o'i da yawa." "Haisam..."ta kirashi a narke. "Akhnan." Shima ya kirata kama yadda suka saba idan akwai sabanin ra'ayi. Sai ya gyara zamansa ya katse ta cikin nutsuwa. "Wannan ba maganarki bane." Ta san muryar nan,muryar da ke nufin ya riga ya yanke hukunci,sai ta jingina da kujerar motar tana hura hanci. "Ni ban gaji ba." Wani dan murmushi ya bayyana a fuskarsa. "Good." Ya fada kawai. Ta dan gyara zamanta. "Ashe zamu iya zuwa kenan." "No." Ya sake amsawa a taqaice. Halinnan ya motsa,na masu tsohon cikin da kusan haushin kowa sukeji. Ta watsa masa wani kallo me kama da harara a fakaice,shi kuwa ya ci gaba da kallon tablet dinsa kamar babu abin da ya faru. Kaman zata saki kuka taji,batason wannan salon nasa.....wani irin salo ne da idan ya yanke abu duk tsaurin idanunka baka iya masa musu. Yana da wani irin kwarjini da badai ka kalli tsabar idonsa ka gaya masa wani abu ko ka musa masa ba.💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 149* Bayan sun isa gida haisam ya tilasta mata cin abinci da hutawa,har sai da ta yi bacci na awa uku. Tana ta farkawa kuwa toilet kawai ta shiga ta wanke fuskarta,ta bulla wani daki ta dauki ruww,bata ma kammala shanyewa ba ta soma lalubensa. Ta same shi a office din nan nasa na cikin gida. Da cikakkiyar sallama ta shiga,ya daga kansa daga wata takarda ya amsa mata yana qare mata kallo. Yadda cikin ke rinjayarta kullum bashi tausayi takeyi,amma ita din kafiyarta da irin jarumtarta na sake burgeshi wani lokaci. Zama tayi saman sofa,har sai daya miqe da zummar kamata amma taka qarasa zama. "Haisam." Ya dago kai. "Mm?" "Na huta." Ya kalleta na wasu seconds bayan ya koma ya zauna. Sai ya rufe file din da yake dubawa. "Good." "Yanzu zamu iya zuwa." Ta fadi tana marairaice masa. Ya san ba zata daina ba,ba zata daina roqonsa ba. Sai ya girgiza kai. "One hour." Idanunta suka soma tara qwalla. "Da gaske?" "One hour." Ya maimaita. "Ita zaki ki dawo." Ta gyada kai da sauri. Ta fahimci idan ba haka tace masa ba,tsaf zaice ba zata ko ina ba sai gobe. Ita kanta ta san ba zata yi biyayya a yau ba. Sosai masarauta ta cika da farin cikin ganinta. Komai ya koma daidai cikin wani irin yanayi da kowa bai taba zaton faruwarsa ba. Wani irin mulki ne qarqashim jagorancin ahmad,wanda yake cike da hikima irin ta sultane da zamananci irin na ahmad din,da kuma shawarwari daga haisam. Mulkin sai ya zama wani iri,kuma na musamman,har yaso yafi na sultane dadi. Me jego falaak na manne da ita. Morsa afiyya ta qi sakinta,kallon akhnan din kawai takeyi tana godewa Allah daya sanya komai yayi farko yana da qarshe. Sultane kuwa ya kasa boye murnarsa shima da zuwan shalelensa. Don ma kunya ta hanata sakewa dashi. Yarinyar falaak tubarkalla,qatuwa fara tas kamar ba daga cikin falaak ta fito ba saboda girma. Ta dade a hannunta ta hanawa kowa ita,har tanajin kamar ta bude idanu taga nata yaran. Sai a sannan taji itama mace takeson haifa,don ita sam basu tsaya tambayar wanne gender bane,haisam din yace kowanne Allah ya bashi yana so,yana maraba dasu. Kaf ta manta dukka sharuddan daya sanya mata na zama ta huta da taqaita zirga zirga,bayan ya amince ya qara mata wasu awannin biyun akan awa dayar farko. Sai data kusa zagaya rabin masarautar,inda duk ta dade bata shiga ba. Ta shiga wani sashe,ta fita wani. Ta je wajen dawakai,dawakanta da tayi kewa,duk da haisam ya siya mata wasu daga qasashe daban daban,amma akwai sabo da kewa me yawa tsakaninta da wadannan. Ta je wajen lambuna,sun jima a ciki ita falaak suna tuna abubuwa da yawa da suka faru a gurin,ciki harda zuwan samarin dake neman aurenta,da ganinta da haisam a guraren na farko. A jikinsa yake jin bata zauna ba yadda yace mata. Da yamma yana cikin meeting da shugabannin tsaro na gidan,daya daga cikin jami'an tsaronsa ya qaraso. "Your Highness." Haisam ya dago kai. "Yes?" "Sun bada tabbacin bata zauna ta huta ba" Sai ya ajiye biron hannunsa. "How long?" "Tunda kuka iso" A hankali Haisam ya lumshe idanunsa. Kwana goma kacal suka rage. Kwana goma zata kwanta a fedeta,amma ta kasa bawa jikinta wannan nutsuwar tun yanzu?. Sallah ta koma yi sashen haisam dake cikin gidan,tana tura bedroom din yana tsaye ya kammala alwala shima zai wuce masallaci. Tun kallon farko ta gane yana fushi. Irin fushin shiru din nan nasa. "Me kuma nayi?" Ta tambaya da salon kama kai irin na wanda yasan yayi laifi. Ya juya a hankali. "Kin huta?" Ta dan yi murmushi tanason boye laifinta. "Eh." "Really?" Yadda ya fadi kalmar ya sa murmushinta ya dan ragu. "Haisam..." Ta kirashi ganin yana neman qureta da wannan narkakkun idanun nasa masu tsananin kwarjini. "Kin zagaye masarauta yau son ranki." Shuru kawai tayi,cikin ranta tana gayawa kanta ashe an kai masa rahoto?. Wanne irin damuwa haka yayi da lamuranta?. Ta dan kau da kai. "Ba wani abu bane me yawa fa." "Kina da tsohon ciki." Muryarsa ta yi qasa da wami nauyi a cikinta. "Kuma kin yi tafiya me yawan da bai kamata kiyi ba right?" Ta yi shiru,shi kuma ya sake zuba mata idanun nan nasa masu girma da haske. A hankali ya qaraso kusa da ita. "Ba zaki kwana a nan ba." Ta daga kai da sauri,ta dauka zai barta ne ganin har ya sake qara wasu awannin. Ta saki jiki zaman gidan ya mata dadi sosai. "Please" Ta fada tana tara hawaye. "Zamu tafi gida tare" "Haisam!"ta kirashi "No."Ya katse ta. "Bana son gardama akan wannan."Ta kasa yarda. "Falaak fa....." "Zata ganki gobe." "Sultane...." "Zaki zo gobe." Dukkaninsu sukayi shuru sannan ya qara da wani irin sanyin murya mai cike da damuwa "Amma yau gida zaki tafi,shine kwanciyar hankalina da nutsuwata." Akhnan ta lura da wani abu a idanunsa. Ba iko bane. Ba tilastawa ba,kaman tsoro ne. Irin tsoron da yake boyewa tun watanni da cikin ta ya fara wani irin girma. Tsoron wani abu ya same ta ko jaririn. Batasan me yasa sam baida jarumta akan komai daya shafeta ba. Rago ne shi sosai ta wannan bangaren ba kadan ba. Sai kawai ta sauke numfashi. Ta san cewa a wannan karon....ba zata ci wannan musun ba. Motar ta bar masarautar cikin shiru. Irin shirunan mai nauyi da ke nufin akwai wanda yake fushi. Akhnan ta zauna gefen window tana kallon hasken Agadez da suke wucewa. Tun fitowarsu daga masarautar bata sake cewa komai ba. Bata kalli Haisam ba. Bata tambaye shi komai ba. Shi kuma ya barta,saboda ya san wannan shirun nata. Har yanzu ba abinda ya sauya sultane,har yanzu goyon bayan haisam yakeyi akan komai. Kaman baiyi kewarta ba kanshi tsaye yace mata tabi mijinta. "Akhnan." Ya kirata bayan ya tabbatar bazai jure shirunta ba. Bata amsa ba,sai kawai ta ci gaba da kallon waje. Wani dan murmushi marar qarfi ya bayyana a fuskarsa. "Habibti." Ya sake kiranta dai bai gaji ba. Har yanzu babu amsa,sai ya mayar da kallonsa gabansa. "Good,at least now I know you're angry." A wannan karon ta juya ta kalle shi. "Ka sani kenan." "Mm." Kasa cewa komai tayi saboda qwallar data sake cika mata ido,sai ta sake mayar da kanta gefe. Shirun motar ya sake komawa kamar da. Har suka isa gida,ya zagaya ya bude mata ta fito,maimakon ta jirashi saita fara takawa ciki tana tura qatoton cikinta gaba,ita a lallai fushi takeyi. Stairs ta nufa kai tsaye,abinda a yanzun indai ya kama zata hau din yana riqe da ita ne,hakanan idan zata sauko shike zame mata madogara. Amma kafin ta kai matakalar farko. "Zauna." Muryar Haisam ta dakatar da ita. Sai ta juya,ya nuna mata kujerar falon. "Please." Ya qarashe fada a nutse. Ta lura da yadda ya fadi kalmar,ba umarni ba ne wannan karon. Sai ta tsinci kanta da dawowa ta zauna a hankali. Gabanta ya matso shima ya zauna sosai. Na wasu seconds yana kallonta ne kawai,kamar yana neman hanyar da zai fara. Ita dince ce ta fara magana muryarta na rawa. "Yanzu zan iya sanin me yasa ka taso ni daga wajen su Sultane kamar yarinya?" Hawayenta suka tsaya dab da idanunta. Numfashi ya sauke a hankali. "Saboda kina daukar kanki kamar baki da ciki." Nan take ta yi shiru,wannan ya bashi dama yaci gaba. "Kin yi tafiya daga wata qasa." Ya daga yatsa daya. "Kin isa gida." Sai ya daga na biyu. "Kin qi hutawa." Na uku. "Kin je masarauta." Na huɗu. "Kuma kin zagaya rabin wurin." Akhnan ta sauke idanunta a hankali tana jin nauyinsa. Yana da wani irin kawaici,yana da wani irin haquri,amma batasan me yasa take saurin hasala haka ba. Ta sani,ba qarya yake yi ba. Jingina yayi da kujerarsa. A karo na farko muryarsa ta yi laushi sosai fiye da kima. "Do you know why I'm worried?"Ta girgiza kai a hankali,sai ya dan yi shiru kafin ya ce "Because there are only ten days left." Akhnan ta dago kai da sauri. "What?" "Ten days."Ya maimaita. "Kwana goma kacal." Ya sake fadi. Ta kafe shi da idanu kamar bata fahimtar yaren French "Kwana goma zuwa me?"Sai ya kalleta kai tsaye. "Kwana goma zuwa ranar haihuwar yaranmu." Wani irin shuru parlor din yayi,sai ta ji zuciyarta na bugawa "Me?" Ta tambaya da tsoro a muryarta. Haisam ya dan matsa kusa da ita. "Likitoci sun riga sun tsara ranar haihuwar,saboda yanayin da suke ganin ya fi dacewa da ke da jariran" Ido ta zuba masa da tsoro sosai. "Kuma baka gaya min ba?" Wani dan murmushi mai laushi ya bayyana a fuskarsa. "Na yi qoqarin hakan." Sai ta tuna.....sau nawa yake son yin wata magana ya fasa. Sau nawa yake kallonta ya yi shiru. Ya kamo hannunta,yatsunsa suka rufe nata gaba daya. "Kin kasance kina gudun maganar cikin tun farko giiftii." Yayi dan shuru. "Ban so na matsa miki ba." Idanunta suka cika da wani irin yanayi. Ba tsoro zalla ba.....ba fushi ba.....sai mamaki da yanzun yafi rinjaye. Kwana goma.....kwana goma kacal?. Kwana goma sai ta zama uwa?..... A karon farko ita ce ta matse hannun haisam,muryarta can qasa sosai. "Haisam..." "Mm?" "Tsoro nake ji." Sai ya dan yi murmushi,irin murmushin da yake yi idan yana son kwantar mata da hankali. Ya dago hannunta ya sumbaci bayan tafin,sannan ya ce a hankali "Good."sai ta hade gira. "Good?" "Because I'm scared too." Akhnan ta zuba masa ido. Da wuya Haisam ya taba yarda yana tsoron wani abu,yau gashi saboda ita taga tsoro qarara a idanunsa. Kallonsa ya sauka kan cikinta,sannan ya dawo kanta. "But we'll do it together......in sha Allah". A wannan karon,akhnan ba ta sake tunanin masarauta ba dama kowa da kowa,sai kwanaki goma da suka rage kafin rayuwarsu ta canza har abada. *_To masu tafiya suna saiku shirya,ku bada list kafin a gama diban adadin 'yan tafiya_*🤒🤒 Nidai na gama nade kayana zanyi gaba,saikun iso.💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 150* *_The Day Three Princes Arrived_* *A Kingdom Reborn* Cikin wani irin yanayi aka kammala dukka bakukuwan. Wani irin biki daya barwa akhnan wani kebantaccen nishadi duk da irin yanayin da take ciki. Ya kuma taimaka wajen dauke mata hankali dan kadan daga tunanin kwanaki goman da suke tunkarota. Tare suka wuce da amare,shehnaz da aisa,wadanda daga kowacce tabi mijinta inda zasu zauna,daga can kuma kowacce zasu wuce guraren da sukafi yawan zama guraren ayyukansu a qasashe da garuruwa daban daban. ★★Safiyar ranar ta zama ta daban kuma ta musamman a gurin dukkanin ahalin motii ibraheem aba jifar,da kuma ahalin sultane muhammad hammud. Safiya ce da dukkanin ahalin biyu ke sanya ran yin idanu biyu da jikokin farko na masarautun.....wadanda zasu sama cikakkun jikoki zalla na jikin motii da sultane. Daga cikin lafiyayyen amenity na asibitin. Giiftii khadeeja muhammad hammud ce,zaune gefan gadon asibitin da aka gyarashi da kyau tun da sassafe da wani irin lallausan fari qal din duvet. Sanye take da silk white robe,wadda tabi jikinta ta kuma fidda dogon cikinta dake gaba wanda sai data tallafeshi da pillow saboda yada take jin yana rinjayarta. Dogon gashinta a nannade a cure a qeyarta da yanayin daya sanya tsayinsa dukka ya bace gaba daya saboda gammo da akayi mata dashi. Hatta da dakin ya sani,yau din wani abu ne na musamman ke shirin faruwa. Saboda kebantaccen daki ne da iyalan motii aba jifar kawai ke kwanciya a cikinsa. Ba dakin kawai ba.....ward ne musamman dan madaidaici da aka ware saboda royal blood na gidan motii aba jifar. Tun daren jiya hannunta yake saman cikinta. Cikin daya kasance tare da ita tsahon wata takwas da kwanaki,cikin da ya canza rayuwarta..... A yau zasu rabu,ba rabuwar baqinciki ba,tana sanya ran zama ta alkhairi da farinciki. Yadda aka jarrabi haisam da son cikin ya sanya take ganin tata qwalamar akan son yaran batakai ko ina ba. Ranar asibitin ya cika da tsaro gaba daya,kamar shugaban qasa ke kwance a ciki. Ranan komai na asibitin ya shaida masu abu da abinsu ne suke cikinsa. Dukkan floor din maternity wing an killaceshi. A hankali qofar bathroom ta bude,haisam ne ke takowa a hankali,gashin kansa dana girarsa,harma da gargasar hannunsa duka jiqe da ruwa. Batasan sau nawa yayi alwala yayi sallah ba daga daren jiya zuwa yanzu. Ta maida idanunta a nutse cikin nasa idanun. Wadannan manyan idanun masu haske,amma a yau sun canza launi kadan,sun kuma rusuna sosai,alamun dake sake bata tabbacin baiyi cikakken bacci ba jiya,bayan ita ya tilasta mata yin baccin duk da bata shirya hakan ba. Dauke idanunsa yayi,ta tabbatar yana son boye mata rashin baccinsa dama karayar da tunda take dashi bata taba ganinta cikin qwayar idanunsa ba irin yau. Tun daren jiya bai zauna ba......batasan ya fita damuwa ba sai yanzu. A kwana taran baya kallon kanta take tana sake mamakin yadda take tsoro take karaya.....amma haisam nan da nan yake maida mata wannan energy din. Batasan ya boye komai bane ya kuma danne sai yanzu,yanzun da mintuna kadan suka rage a shiga da ita Cs din. "Haisam." Ta kirashi da yanayin da tasan yafi so. Sai ya waigo kamar yana jiran kiranta. "Ka zauna." Ta fada tana jin tausayinsa yana narkar da zuciyarta. Iya wannan kawai ya sanyata dagewa da addu'an Allah yabar masa ita da yaran duka a raye. "Ina zaune tun dazun ai" "A'a." Ta girgiza kai tana sakar masa murmushi. "Kana sintiri dai yarima na" Karon farko a ranar dan murmushi ya bayyana a fuskarsa. "You're enjoying this." Ya tambaya yana dage mata girarsa duka biyun. "A little." Ta fada tana kashe masa ido daya still da murmushi a fuskarta. "Good." Ya fada yana warware hannun shirt dinsa daya nade saboda alwala. Ta dan bishi da kallo,yau shigarsa ma,irin shigar da ba kasafai ya fiya fita da iya bane. Farar t-shirt ce qal da baqin trouser daya haska har saman dogayen yatsun qafafunsa. Ya mata wani irin kyau,sai takejin kamar a qara mata lokaci tare dashi tayita kallonsa. Qarasowa yayi ya durqusa a gabanta. Ya dora hannunsa kan cikinta. A hankali ya motsa labbansa,bayan ya matso dasu kusa da tsinin cikin. "Behave yourselves today." Wata tattausar dariya ta saki "Wa kake wa magana?" Ta fada idanunta a bude tana kallon wannan calm face din nashi. "My sons." Ya bata amsa da calmness dinsa da baya taba barin jikinsa komai girman tashin hankali. "Who said they're boys?" Ta fadi tana bata fuska,don ita har ga Allah baby girls tafi sha'awa. Tunda ta dora idanunta akan baby falaak da taci sunan morsa safiyya suke kiranta da sultana,taji duk duniya baby girl takeso. "Ku bani ita don Allah" Tace da maleek a daren sunan daya samu shigowa ganinsu. Murmushin nan nasa me harba jinin sarauta a jikinsa yayi,ya kalli falaak kawai. "Idan ta baki nima na bayar" Saita falaak ta fidda ido waje tana dariya. "Zai hadamu fada ne kawai giiftii". Haisam da yake can gefe yana amsa waya ya jisu,bai amsa mata ba sai da suke tattaki suna komawa sashensu. "Abinnan fa da kikace zaki kira sultane ki gaya masa anyi shi akayi aka samu yarinyar nan....banda anyi hakan da falaak din taki tana nan zaune ita daya ba sultana din.......amma yanzu duk bayan kince zaa kashe miki sisinki kuma an mata gata da baby kice su baki?" Kunya ta kamata,wata irin kunya me nauyi data tuna wautarta a wancan ranar. Allah ya taimaketa daya taka mata birki,da da wanne ido zata dinga kallon sultane a yanzu?. "Eh....amma har yanzu abinnan dai kasan abun jin kunya ne ko?" "Eh.....duk da hakan kuma baki fasa tashi na jiya kince saina miki ba ko" Qaramin ihun kunya ta saki tana cusa kanta a qirjinsa data tuna da dabarun da aka samu akayi saboda yadda tsaho da tudun cikinta ke hana komai. "Allah ya tabbatarmin dake a haka ko kin haihu" Taji yana fada qasa qasa cikin nishadi. "They are." Amsar haisam ta maido da tunaninta kansa. "And if they're not?" Ta fada tana turo baki gaba. "They are." Ya sake maimaitawa kyawawan idanunsa suna lumshewa gami da budewa. Kukan shagwaba ta sakar masa,ya miqe yana sakin siririn murmushi gami da fara cire mata dan kunnen dake kunnenta. "Fadata ai ba fadan Allah bane ko?" Sai daya fadi hakan sannan ya samu sauqi. Shi ya shiryata tsaf cikin kayan daya kamata ta kasance a cikinsa. Wani irin shiru ne ya mamaye private wing din asibitin. Ba shiru irin na rashin mutane ba. A'a.....shirun da ke zuwa kafin wani babban al'amari. A cikin waiting parlor din dukkaninsu suka dakata,don haka ba wanda akhnan tasan da zuwansa. Basason su kasance tare da ita tunda wuri haka,saboda karsu kaya mata zuciya,shi yasa ta dauka daga ita sai haisam dinne kawai a gurin. kowa na qoqarin boye damuwarsa. Daga bangaren kujerun dama nanay ce,zayne riqe da tasbaha. Labbanta na motsi da addu'ar da bata saketa ba tun daga ranar da haisam ya gaya mata Cs din akhnan. Morsa Safiyya na zaune kusa da ita,Idanunta na kan qofar da akhnan zata fito. Ta kasa tantance wanne matsayi take kai,gaba daya ma sai taji kaman addu'ar na shirin qwace mata. Sultane yaso ta zauna gida saboda falaak,amma ita kanta falaak din sai da akayi da gaske sannan ta zauna din. Daga daya bangaren sultane dinne,zaune yake cikin nutsuwa,amma duk wanda ya san shi zai gane cewa yau zuciyarsa ba cikin nutsuwar da yake nunawa take ba. Hussam na kusa dashi shi da Aareef,sau noorah dake zaune gefan morsa safiyya. A nutse akhnan da haisam suka fito daga dakin,magana yake gaya mata qasa qasa wadda ba wanda yasan me yake gaya mata sai ita dashi. Cikin doguwar farar rigar asibitin take takowa,hannunta cikin na haisam din. Mamaki ya saukar mata ganin dukkaninsu a zaune a gurin,ba tare da sanin isowar kowa a cikinsu ba. Ta bude ido da baki dukka tana takowa,sai dukkaninsu suka hutar da ita ta hanyar tasowa suka risketa. Gaidasu taketa qoqarin yi,amma sukam ba wannan bane a gabansu. Yadda cikin ya qara qasa yadda take takawa da qyar kowa ke tausayawa. Addu'a ce kawai ke tashi a gurin,ta wani tana shiga cikin na wani,haisam na tsaye daga baya yana amsawa daya bayan daya. A lokacin ne kuma nurse ta iso da wheelchair. "Madam, we're ready." Ta janyo wheelchair din kusa da akhnan din. Kallonta akhnan din tayi,sai kuma ta kalli wheelchair din. Ta girgiza kai a hankali. "No." Ta fada a sanyaye. Murmushi nurse din tayi,tana zaton ba ta ji ba ne. "It's okay. We'll take you comfortably." Ta fada cikin girmamawa. Kai akhnan ta sake girgizawa. "Ba zan hau ba." Ta maimaita mata wannan karon da yaren oromo yadda zata fi fahimta. Mamaki ya kama nurse din,ta dan rusuna sannan tace "But......" "I can walk." Ta dakatar da ita ta hanyar qarasa mata bayanin. A nutse ta janye dubanta,sai idanunta suka koma kan haisam. "Ina son muyi tafiyar tare." Ta furta a sanyaye idanunta cikin nasa. Wata irin nutsuwa ta ratsa fuskar haisam,kamar ya fahimci abin da take nufi. Ba maganar tafiya ba ce kawai. A'a.....tafiya ce ta qarshe da zasuyi kafin su zama iyaye ita dashi. Ya matse hannunta a hankali yana sake nutsa idanunsa cikin nata. "Are you sure?" Ta gyada kai. "Very sure." Ta amasa masa tana qoqarin maye gurbin tsoronta da murmushin. Sai ya dan sunkuyar da kansa da yanayi na girmamawa tamkar yana magana da motii. "Then we'll walk." Ta bata tabbaci tare da wani confidence na daban. 💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 151* A nutse nanay ta share hawayen da suka cika idanunta. Wata irin qauna take gani wadda take kafa kanta da kanta,take kuma kafa tarihi,koda ba'a gaya maka ba idan ka gani kasan cewa sun manta da kowa,sun manta da komai sai kawunansu. "Allah Ya tsare ku." Nanay ta fada a fili. A hankali akhnan ta qarasa gare ta,ta saka hannuwanta suka ta rungume nanay din,rungumar da batayi yadda taso ba saboda cikin gabanta. Rungumar da ta sa Nanay ta qara riqeta,kamar ba ta son sakinta.kamar rumaisa ko Aaani ne zasu shiga dakin tiyatar. A yadda takeji a yanzun,batajin idan su dinne ma zataji hakan. "Ki dawo min lafiya diyata." Nanay ta fada cikin rawar murya "In sha Allah." Ta amsawa nanay da jarumta sosai a muryarta. Sai ta matsa wajen morsa Safiyya,morsa safiyyan da ta riga ta fara kuka tuni. Ta kasa jurewa,idan har wani ke rubuta qaddarar wani,zatacw bata taba hango akhnan din zata iya daukar ciki me girma irin wannan dake jikinta ba a yanzu. "Sannu da qoqari biftu....sannu da ibada." Akhnan ta yi dariya kadan cikin jin nauyi. "Ni kuma bana son kina kuka." Qoqarin shanye kukan tayi ta janye jikinta kadan tana son bawa kanta qwarin gwiwa. "Ki dawo da kishiyoyina ko masu gidana lafiya qalau" "Ana gudun kishiya kuma kina nemanta momma" Akhnan tadan tsokaneta kadan. "Eh,to wadannan su kam ya zanyi dasu?." Ta fada tana qarasa goge fuskarta. Duk suka yi dariya. Ko da cikin damuwa ne,amma hakan ya sake rage musu tension. Daga nan ta juya zuwa ga Sultane,na dan lokaci suka tsaya suna kallon juna ita dashi. Wannan qaunar ta daban dake tsakaninsu kana iya ganinta cikin idanunsu. Sultane ya daga hannunsa ya dora shi saman kanta. "Allah ya sanya albarka a abinda zaki samu biftu.....Ki dawo mana da farin ciki in sha Allah" Qwalla taji ta taru a idanunta,aai ta gyada kai kawai. Ba ta yarda ta yi magana ba,saboda ta san idan ta yi hawaye ne zasu zubo. Kuma ta yiwa haisam alqawari ba zatayi kuka a gabansu ba. Koda zatayi kukan,zata yishi ne a jikinsa.....a kafadarsa.....a gabansa shi kadai. Juyawa tayi tana maida hannunta cikin na haisam. Ba wheelchair. Ba gaggawa. Kawai su biyu. Miji da mata. Masu tafiya zuwa lokacin da zai canza rayuwarsu har abada. Corridor din yayi tsawo,amma babu wanda ya yi magana na wasu daqiqu tsakanin ita ko shi. Ita ta fara matsawa sosai kusa da shi. "Haisam." "Na'am." Ya amsa mata yana qoqarin kore damuwa. "Kar ka firgita idan na firgita." Ta fada a sanyaye. Sai ya yi murmushi kadan,wancan murmushin da ita kadai take iya fitowa da shi saman fuskarsa. "Too late." Ya furta ba tare daya kalli fuskarta ba. Murmushi me sauti kadan tayi. "Kana tsoro ne?" "A lot." A yau ya bata amsa kai tsaye ba wani kwana kwana. Ta dago kai ta kalle shi tana jin amsar tasa har cikin zuciyarta. Mutumin da yayi hannun riga da tsoro......amma a yau yana bata tabbacin tsoro kai tsaye daga bakinsa. "Ni kuma bana tsoro." Ta furta kai tsaye. "I know." Ya amsa a wannan karon yana maido dubansa kan fuskarta. "Why?" Ta tambaya taba rungume hannunsa sosai,sai ya tsaya na dan lokaci daga tafiyar da sukeyi ya kalleta da kallon da ya saba yi mata tun farkon soyayyarsu. "Because you're stronger than all of us." A wannan karon,hawaye suka cika idanunta. Kafin ta samu damar amsawa suka isa qofar theatre din. Ta dauka zai tsaya ne kaman yadda kowa keyi daga waje,amma sai taga suna shiga tare dashi. Wani irin sanyi da farinciki ya mamayeta. Bata fahimci yana gurin za'ayi aikin ba sai da taga sun bashi medical gown yana sakawa. Ta lumshe ido tana kallonsa sanda yake daure rigar a jikinsa. Ta masa kyau.....sosai,wani irin kyau daya haska har cikin qwayar idanunsa. Hannunsa cikin nata suka mata anesthesia suka kwantar da ita,sai suka ajiye masa kujera kusa da kanta ya zauna idanunsa cikin nata. Shi da ita dukka suna jin maganganun likitocin da zasu mata aiki wadanda dukansu mata ne,sai anesthesiologist namiji da wani guda daya daban da bazaizo kusa da ita ba. Ko sau daya bai bari idanunta sun huta daga kallonsa ba.....tana jin sanda aka soma yaga fatar cikinta cikin nutsuwa da takatsantsan. Ta daga idanunta tana kallonsa sosai. "You look pale." "I don't." Ya fada da murmushinsa dinnan me taushi yana juya kansa kadan. "You do." Ta maimaita masa tana son yin dariya. "Focus on yourself." Ya fada yana dan lakuce mata hanci da yatsansa. Murmushi ta sauke "Allah you are scared." "I'm not......giifii mana" Ya fada yana dan yamutsa fuska yadda take masa idan ya dameta da tsokana. Likitar ta yi dariya,don duk maganan da suke tana jinsu. Komai nashi asali burgeta yakeyi,a yanzun da taga mu'amalarsa ta zahiri da matarsa sai abun yake sake burgeta qwarai. Ta girme masa nesa ba kusa ba,amma tana yabawa halayensa sosai. "Your husband is definitely scared." Itama ta sanya musu baki. A karo na farko akhnan ta ga ya kasa musantawa. "Can everyone stop discussing me?" Ya fada yana basarwa sosai,abinda ya bawa kowa na dakin dariya,dariyar kuma ta cika dakin.....ta rage mata tsoro. "Hold my hand tighter" Akhnan ta fada da muryar rada. Idanunsa cikin nata ya sauke mata wani murmushi me laushi,ya kuma sake matse hannun nata cikin nasa. Abinda ya lura,yadda yake qoqarin bata aminci.....itama dake kwance cikin irin wannan yanayin qoqarin bashi nutsuwa takeyi. Lokaci ya ci gaba da tafiya a hankali,yana debo mata memories din rayuwarsu ta baya. Wani tayi murmushin kunya wani ta musanta kadan ba hayaniya ko motsi me qarfi. Doctors suna aikinsu,komai na tafiya yadda aka tsara. "Remember madeena?" Ta dan yi mamaki. "Yanzu?" Saboda bata dauka labaransa zasuyi tsaho haka ba,kwata kwata ya hana tunaninta komawa kan Cs din da ake mata a yanzu haka,yanata daukarta yana cillata wasu duniyoyi. "Yes." Ya amsa mata,sai ta yi dariya a hankali. "Me yasa?" Ta sake tambayarsa,ya dan yi shiru kafin ya ce "Saboda a lokacin ne na fara gane....." Sai ya dakata kaman yana ja mata rai,ya saba mata irin haka idan yana bata labari,sai suyita rigima. "Gane me?" Ta tambaya da zumudi Idanunsa suka sauka a kanta da wani laushi. "That I was already in trouble." Ta hade gira. "Wane irin trouble?" Sai ya dan matsa yatsunsa dake cikin nata. "The kind where a man stops thinking about himself." Akhnan ta ji wani irin abu ya taba zuciyarta. Inde zai magana da ita irin haka,sai ya sake matsa zuciyarta da soyayyarsa. Ko yanzu.....a irin wannan lokacin......har yanzu yana qoqarin rage mata tsoro,bai barta da firgici ko damuwa ba. Sai kuma wani motsi ya sauya yanayin dakin. Likitocinne suka fara magana da juna cikin farinciki a muryarsu. Akhnan ta juya kanta kadan,bata fahimci komai ba tukuna. Saidai a take qaramin sauti ya cika dakin. Rauni sosai a muryar dake son nuna jarumta da qwazo......sabon sauti ne.....mma ya isa ya sauya komai. Hawaye taji sun cika idanunta kafin ma ta sani. Ta sake juya kai zuwa ga haisam. Fuskarsa ta sauya gaba daya,kamar mutumin da aka cire masa duniya aka ba shi wata sabuwa. Bata taba ganin irin wannan fuskar tasa ba. Fuskar dake shimfide da wani sabon farin ciki tsantsarsa. Sai ya lumshe idanunsa na dan lokaci,kamar yana godewa Allah a ransa. Da ya sake bude su....suka hadu da na akhnan. Kasa magana yayi,don yaji kawai ba'a buqatar kalmomi. Sai ya daga hannunta ya sumbaci bayan tafin hannun a hankali,sannan cikin murya mai rauni da ba ta taba ji daga gare shi ba yace "Thank you,akhnan." Hawayen da take qoqarin hanawa suka zubo jin wani sabon kukan bayan wancan daidai sanda haisam ya gama kissing hannun ta yabar mata wani abu me taba zuciya. Ta yi murmushi a hankali a lokaci guda,saboda a wannan lokacin....ta san cewa ko bayan shekaru masu yawa ne.....idan ta tuna wannan rana. Abin da zata fi tunawa ba tsoro ba ne. Sai yadda haisam ya kalleta.....kamar ita ce kyauta mafi girma da Allah ya taba yi masa a kaf rayuwarsa. "Wait." Muryar likitar ta ratsa dakin. Dukkansu suka tsaya kafin a hankali daya daga cikinsu ya kalli monitor. "Doctor..." Ya kirata Wani irin shiru ya ratsa dakin. Kamar ita kanta ba ta yarda ba likitar dake duba cikin akhnan din. "I think..." "...there's another baby." Miqewa tsaye kawai haisam yayi,har yanzun dai bai saki hannun akhnan ba,amma mamakin da yaji yana juyashi sam sai yaji bazai iya zama ba. "There's another baby." Ta sake maimaitawa sanda ta tabbatar. Zaro ido akhnan tayi "Another baby?!" "We were told twins." Haisam ya fada yana jin yau duka kaman jarumtarsa ta qare. "So were we." Likitan ta fadi itama. Har yanzu yana tsaye,kamar an dakatar da tunaninsa,har zuwa sanda daya daga cikin nurses ta zagayo ta kawo masa daya daga cikin jariran da aka gama gyarawa. A hankali ya karbe shi......ya karbeshi da hannayen nan nasa. Hannayen da suke riqe na'urori domin binciken tabbatar da gaskiya. Hannayen da suka rattaba manyan yarjejeniyoyi. Yanzu kuma... Sune suke riqe da jariri. "All yours." Nurse din ta fada tana nuna masa bangaren da guda biyun ke kwance ana gyarasu suna sake rikita dakin da kuka. A nutse idanunsa suka koma kansu. Na farko. Na biyu. Na uku. Sai ya yi wata irin murmushi me sauti qasa-qasa. Wannan murmushin da akhnan bata taba ji daga gare shi ba. Idanunsa ya maida kan yaron a hankali. Kyakkyawar halittar me wani irin kyau da shiga zuciya. Komai nasa qanana masu kyau da daukan hankali,da kamannin da baisan da baisan na waye ba shimfide saman fuskarsa. Shi ko akhnan. Wata irin qaunarsa ta farat daya ta soma shiga zuciyarsa,qaunar daya tabbatar ashe sanda yana cikin akhnan qaunar bogi ce yayi musu,yanzunne yake ta haqiqa da gasken gaske take shiga. Da kansa ya taka ya kawo matashi saitin fuskarta. "Twins ko?" Ta fada tana son samun tabbaci. Haisam ya sauke idanunsa a kanta,sai ya girgiza kai a hankali. "Apparently not." Ta yi dariya cikin hawaye tana jin yadda zuciyarta ke bugawa da qaunarsa shi da abinda yake riqe dashi da sauran 'yan uwan da bata gani ba. Shi ma yayi murmushi. Sai ya matsa kusa da ita,ya sumbaci goshinta,sannan ya rada mata "Akhnan..." "Mm?" "Next time..." Ta daga gira,sai ya kalli jariran uku. "...we're discussing this with Allah first." A wannan karon har likitocin suka yi dariya. Yadda komai nasa ke cike da nutsuwa.....komai nasa ke cike da addinin nan da kowa ya sanshi dashi. Wani miji na daban suma suke gani,wanda ya sanya sukayi wata irin tiyata me sauqin da basu taba irinta ba.💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 152* Ya tayasu sun mantar da matarsa a inda take ba tare da allurar bacci ba. Kallo kulawasa kaffa kaffa dake cikin idanunsa a kanta na dabanne,ba irin wanda suka saba gani a idanun kowanne magidanci bane. A gurin....sun sake ganin wata fuska tashi ta daban,da duniya bata san da ita ba. Wani sassauqan yarima.....wanda farincikin iyalinsa.....kulawa dasu ya sanyasu sama da komai nasa. Akhnan kuwa ta kasa daina murmushi,idan ta tuna ba twins ba ne. Ba kuma daya ba ne......Allah ya ba su fiye da abin da suka yi tsammani,sai taji kamar sa'arta ta kere ta kiwa a rayuwa. A wajen theatre dukkaninsu sultane jira sukeyi. Sanda qofar ta bude nurse din ta fito don ta musu albishir dukkaninsu sukayo kanta. "Ya suke?" Dariya tayi cikin nishadi. "They're fine." "They?" Hussam ya fada yana matsowa kusa da imda nurse din take tsaye. "All three of them.." "Three?" Morsa safiyya ta fadi da wani irin tarin mamaki a fuskarta. "Three?!" Noorah itama ta sake fadi tana sakin qaramin ihu. "THREE?!" Hussam ya sake fada yana qara fidda ido sosai. "Three healthy boys" Nurse din ta sake jaddada musu albishir dinta na farko. Morsa safiyya ta fashe da kuka. A wannan karon ba ta iya tsayawa ba. "Alhamdulillah..." Kusan dukka bakunansu ke furtawa. Sultane ne ya janyeta yana lallashinta,kafin ta nutsu ta zauna. Tana kuka tana dariya lokaci guda,wanda bata taba sanin ana hakan ba sai a kanta.....a kanta a yanzun. A cikin dakin kuwa an gama komai. An shirya akhnan da duka yaran zuwa dakin hutu. Sannan aka kawo yaran kusa da ita. Ta waiwaya a hankali tana duban qananan fuskoki uku. Qananan hannaye uku. Ta kasa magana,kawai kallonsu takeyi,sai ta waigo ta kalli haisam,nan ma ta tarar shima kallon yaran yakeyi kamar wanda aka cire masa numfashi. "Haisam." Bai amsa ba. "Haisam." Ta sake kiransa. A hankali ya kalleta,Idanunsa sun sauya launi da yanayin dake nuna yanayin ya taba jikinsa sosai. "Yan uku." Ya maimaita a hankali "Three." Ta sake maimaita masa,sai ya yi murmushin da ba kasafai ake gani ba. Murmushin farin cikin da ya fito daga zuciya. "Allah has a sense of humor." Sai ya kama hannunta. Ya sumbaci bayan hannun. "You gave me a kingdom." Ya fada da wata murya me kama da rad'a. Lallausan murmushi tayi cikin hawaye,tana jin wata falala da ni'ima daga Allah tana lullubeta. A ranar ba kamfanoni ba ne. Ba dukiya ba ce. Ba sarauta ba ce. Abin da ya fi komai muhimmanci ga haisam shi ne matarsa da kuma qananan yaransa uku da Allah ya ba shi lokaci guda. Kyautar da baiyi zato ba. Daya bayan daya ya daukesu,yayi musu huduba kaman yadda addinin musulunci ya tanada. Tana daga kwance bacci yanason kwasarta,amma shine a idanunta. Shi da yaranta. Shi dasu kewaye a gabansa yana daukarsu daya bayan daya. Ko sanda zai gama musu hudubar bacci yayi awon gaba da ita. Ya taka zuwa gabanta a nutse ya tsaya murmushi yana fita daga fuskarsa. Ya dora hannunsa saman sassalkan gashinta me tsaho da santsi da hular dake kanta ta zame saboda santsin gashin. Ya tsugunna a hankali yayi kissing goshinta. "Allah yayi miki albarka" Ya maimaita har sau biyu yana jin yadda soyayyarta take ratsa zuciyarsa da wani sabon babi da muhalli na daban. Yinin ranar gaba daya asibitin ya zama wani guri na zirga zirgar jama'a. Familyn motii aba jifar gaba daya a hautsine yake da murnar samun yara uku lokaci guda. Yaranma wadanda suka fito ta tsatson yarima muhammad haisam. Batasan gata suna ya tara ba sai yanzu.....batasan gara a rayuwa hawan hawa bane sai bayan data haifi yaran. Zamanta a asibitin ya sanya ta gane a baya qaryar gata take. Zamanta a asibitin ya sanya ta gane tsananin zurfin son da haisam yake mata wanda a baya bata gama fahimtarsa ba ashe kwata kwata. A zaman asibitin ta sake yarda dashi da dukka komai nata. A zaman asibitin taga other side dinsa cikin kwanaki uku kacal. Baya kunyar kowa a kanta,baya shakka ko kowanton nuna mata kulawa. Baya barin kowa da hidimarta. Komai shike mata,abinda ya sanya ta sake tsinkewa da lamarin. Idan ka ganshi zakayi tunanin ba shine wannan yariman ba.....ba shine mamallakin manyan kamfanunuwan turare......fitaccen malamin nan.....jinin sarauta daya tara dimbin ilimin addini dana boko ba. Hatta da saka drip allura bada magani dake wuyan nurses ya azawa kansa shi. Kome yake idan lokaci yayi zaka ganshi ya iso asibitin ya shigo dakin. Ko a gaban waye zai dauki yaransa ya rungumesu,ya gaya musu yayi missing dinsu. Zai matsa gaban gadon,zai riqe hannuwanta,zai gaya mata yayi kewarta,zai kuma tambayeta dame dame tayi sanda baya nan?. Dame dame take buqata a yanzun?. Cikin yaran waye yayi kuka?,wayi yayi bacci sosai?. Bame zazzabi?,bame wata damuwa?,idan kaga yadda yake tambayar komai daki daki sai ka dauka ya jima basa tare,kaman tazarar kwanaki ne suka raba tsakaninsu ba 'yan qananun awanni ba. Yawancin lokuta yana shigowa dakin kowa ke fita ya basu guri. Cikin kwanakin wani abu daban take gani a qwayar idanunsa da ya ninka wanda take gani a baya. Kwana uku kawai.....amma ya zame mata wata duniya ta daban. Ya bar mata tarin memories da har abada ba zasu taba shafewa daga rayuwarta ba. Batasan adadin mutanen data gani ba masu zuwa marabtar yaran.....a hakanma asibitin da haisam sun iyakance adadin masu ziyara a kullum. Har a ranar da suka cika kwana ukun bataji komai game da sunan yaran ba. A ranar ne kuma group na 'yan shidansa suka iso asibitin dukkaninsu a tare don ganin yaran. Yana dakin a sannan,yana zaune a gabanta,ya tsirata da idanun nan nasa yana bata magani tana karba tana sha da qyar. Ya rasa wanne irin rashin jituwa ne tsakaninta da magani,ita kuma ya mata kwarjinin nan nasa da bazata iya musa masa ba. Allah ya taimaketa daya daga cikin yaran ya farka,ya tashi kuwa kuka sosai dake alamta yunwa yakeji. Tsam ya miqe zuwa gadajensu,wani irin gado me kyau hade da rumfar da bazai bawa ko qura daman shiga ba bare wani abu na daban. Da murmushi a fuskarsa ya ciroshi yana rarashinsa kamar me magana da babba. Daya daga cikin abubuwan da idan yanayi yake sanyata tattara hankalinta gaba daya tayita kallonsa riqe da yaran. Ya qaraso gabanta,ya tsaya dab da ita har tana jin saukar wannan lallausan qamshin nasa. Sai daya tabbatar da nutsuwar yaron sannan ya daga idanunsa ya sauke a nata. "Gyara ki feeding nasa" Idanu ta fiddo tayi narai narai. Ta yaya zata fara haka a gabansa?.. Yaci gaba da kallonta yana karantar reaction dinta. "Eheennn" Ya sake fada yana dubanta. Ya jima yanaso yaga yadda take shayar da yaran,amma saidai ko sau daya a kwanakin bata bari ta basu a gabansa ba,tunda ana hada musu da madarar yara kafin jikinta ya qara daidaita. "Haisamm" Ta fadi ganin yana matsowa dab da ita ya miqa hannu yana qoqarin zuge zip din gaban rigarta. Idanu ya zuba mata yana kallonta,saidai kafin yace komai ta zame hannunta daga saman nashi a hankali,ta rufe idanunta tana jin yadda iska ke ratsa fatarta alamun ya zuge zip din gaba daya. Sai da yaji wani abu ya tsarga masa tun daga tsakiyar kansa zuwa tafin qafarsa sanda idanunsa ke sauka a kansu. Farare tas sun cika sosai,suna tsaye kuma kamar yadda ha sansu. Ya lumshe idanunsa a hankali sannan ya budesu,ya matsa yana dora mata shi saman cinyarta ta hannun damanta ya sanyata ta daidaita zamanta. Tana jin sanda ya saka hannu ya ciro masa ya saka a baki,tana jin yadda yaron ke cin abincinsa.....tana kuma jin sanda ya koma kawai ya zauna ya zuba mata idanu yana kallonta ita da yaron gwanin sha'awa. "Me zai hana.....kowanne shayarwa kimin alfarma" Sai ta bude idanunta a hankali a kansa. ".....kiyi alwala kafin kowacce shayarwa" Ya qarasa maganan da alamun akwai abinda yakeson ya sake cewa. Amma bai samu wannan damar ba,noorah da tunda akayi haihuwar ta tare a asibitin ita da camera dinta tayi knocking. Ya bata izinin shigowa,ta shigo da lallausan murmushin nan nata tana cewa.. "Obboo.....yaa maleek......ya khadeem......" "......da omar" Ya qarasa mata. Kanta ta gyada da murmushi,sai ya miqe a nutse yana duban akhnan. "Birra zata shigo,ki shirya please,banason kowa yaga komai.....inkin kammala shayar dashi ki fadamin sai mu shigo" Sai ya matsa yayi kissing goshinta yana janyewa da baya a hankali idanunsa a kanta ita da yaran gaba daya,sai kuma ya juya yana ficewa da wannan takun nasa me cike da qasaita yana daga wayarsa data fara ruri,wanda da alama kira ne daga su omar din dake waje suna jiran a musu iso.💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 153* _________________________ *_INGANTACCEN MAGANIN SANYI NE SADIDAN,WANDA BA'A CAKUDASHI DA KOMAI BA SAI ZALLAR SASSAQE DA ITATUWA MASU AMINCI_* *_KAYAN GYARA MASU INGANCI DA WARWARE MATSALAR MATA TA FUSKAR CIWON SANYI WANDA YA KASA JIN MAGANI_* *_GARZAYA A SIRRANCE KI WARWARE MATSALARKI,KI TUNTUBETA TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE_* +234 810 914 9876 __________________________ Ajiyar zuciya ta sauke a hankali,ta maida idanunta saman fuskar yaron dake shan madararsa a hankali. Ga mamakinta kamar yasan fuskarshi take kallo sai ya riqe yatsanta gam cikin nasa da nata yatsan. Ba shiri murmushi ya subuce masa,ta zuba masa idanu tana kallon yadda hankalinsa ke kwance a jikinta. "Ko yaya sunanshi?" Ta tambayi kanta,daidai sanda birra ta turo qofar dakin tana shigowa. Fuskarta dauke da murmushi,idanunta akan gadon yaran kamar kullum kafin ta dauke idanunta ta maida kan akhnan. "Yarima yace nazo na gyaraki....akwai baqi zasu shigo" Ta fada da girmamawa da kulawa. "Bari na kammala bashi tukunna" Matsowa tayi daura da akhnan din,tana kallon babyn dake kan cinyarta. Duk bayan sakanninsai ta gyarawa akhnan daukan yaron,idanunta da hankalinta dukka suna kansu. Ta daga kai ta kalleta sanda take karbarsa daga hannunta ta dorashi a kafada don yayi gatsa. "Birra" Ta kirata wanda ba Kasafai take hakan ba. "Na'am" Ta amsa tana dubanta. "Inaso ku fitar da miji ke dasu buhaina......aure zan muku" Ta fada kai tsaye. "Aure?" Ta tambaya tana fidda idanu waje. "Eh aure,yara mata ne ku da kuke da chance na aure da haihuwa kamar kowacce diya mace,bai kamata ku zauna kawai rayuwarku ta qare a haka ba". Wata kunya ta gani cikin idanun birran,sai ta sunkunyar dakai tana takawa zuwa gadon da sauran 'yan uwanshi suke ta kwantar dashi a cikinsu,sannan ta dawo ta taimakawa akhnan din ta rufe jikinta da wata kyakkyawar after dress mara nauyi. Ta juya ta fita don sanarwa da haisam sun kammala. Tun daga nesa ta fara jiyo muryoyinsu,daura da dakin da 'yar tazara kadan.Tun daga corridor din,dariya.....tsokana.....hayaniyar tsaffin abokai da wani irin aminci da yarda da juna da kuma shaquwa me zurfi suka shiga tsakaninsu. Muryar omar tafi ganewa,don muryar tasa ma tafi ta kowa fitowa. "Move" Taji Omar din yace. "Kai.....kabi guy dinnan a hankali,yanzu ya fika matsayi.....he can throw you out ya hanaka ganin babies dinka". Tuni akhnan ta fara murmushi,Saboda ta san wadannan mutanen,wadannan 'yan shidan....kullum idan suka hadu zaman lafiya kuma ya qare. Sun yita dauki ba dadi a tsakaninsu. Ba can baya da suke zamartaka ba,har yanzun da kowannensu ya zama mahidanci ma,gashi har sun fara tara 'ya'ya. Qofar ta bude a nutse,kaman ba sune take jiyo hayaniyarsu daga corridor ba. Haisam ne a gaba,kamar wanda ke jagorantar wani taro na musamman. Idanunsu suka hadu da nata,murmushinta ya qara fadada. Yau kam zata ga yadda zaiyi.....mutumin da baison cikakken hayaniya ko doguwar magana. Yau ga 'yan shida ciwon kansa kenan,batasan ya zasu qarke ba. Maida mata yayi,ya mata magana da ido dake nufin "Bari kiga wannan rigimar" "Behave yourself" Yayi maganan yana shan mur. "We're not children fa captain sheikh....." ".....gaya masa,speak for your self captain" Dariya yayi,irin boyayyar dariyar nan da saidai tasa fuska kawai ta washe. Daya bayan daya suka fara shiga,dukansu cikin tsari....classy...legant. Da wannan nutsuwar da kamar dukkaninsu sun samu tagomashinta. Kana kallonsu kaga matasan dake tafiya kafada da kafada da nasara. Irin matasan da sukasan kansu suka kafa duniyarsu arziqinsu da komai nasu da ilimi nutsuwa da halal cikakkiya. Kowanne sai da yayi sallama sanda suke shigowa. Haka ta amsa musu daya bayan daya suna neman sofas din da aka ajiye daga can gefan dakin saboda zuwan baqi irin haka. Daya bayan daya suka gaidata,abin daya sanyata jin nauyi da kunya kenan. Su kam wai suna mantawa ne da matsayin da suke dashi a idanun duniya?. Me yasa suke da sauqin kai har haka dukkaninsu,wanda idan daga nesa ka kallesu sam basuyi zubi ko kama da mutane masu sauqin kai haka ba. Ta dauka zata ga su khadeem dasu shehnaz,tunda tunda ta haihu wayarta na ajiye,amma sai ta kasa tambaya. Omar ne kawai basu gaisa ba,don haka ya matso gaba kadan. "Sannu da jiki, Princess." Akhnan ta amsa da murmushi. "Nagode." Ta furta da murmushi tana tuna wasu abubuwa. Tana tuna sanda ta fara sanin da zaman sheikh haisam cikin masarautar agadez. Tare ta sanshi da omar. Omar din kuma shi kadai ne take ganin wargi wani lokaci a idanunsa,amma badai haisam ba. "Wallahi ka bamu tsoro." Mutallab ya fada yana,nan take Haisam ya daga ido ya kalle shi. Daga hannuwansa mutallab din yayi. "I'm serious!" Ya fadu kansa tsaye sannan ya kalli Akhnan. "Mutumin nan ya hana mu sakat." Akhnan ta dan yi dariya tana aza idanunta kadan kan mutallab. Ya tsare mutallab din da ido,saidai a yadda ta fahimta sai mutallab ya gama fadin albarkacin bakinsa bazaiwa haisam shuru ba kaman yadda yakeso. Omar ya gyada kai. "Three days." Ya nuna haisam. "Three days yana kiran likitoci fiye da yadda yake kiran mu?." Dariya duka suka sanya masa,akhnan ma tayi qasa da kai tana boye tata. "Harda ke?" Ya fada da sigar tambaya yana dage dukka girarsa sama hannuwansa harde qirji. "No....ba laifina bane..." Ta fada tana qoqarin hadiye dariyar. "Wait....." Amjad ya fadi wanda tuni yakai bassinet din da yaran ke ciki. Juyowa yayi garesu,sannan ya maida dubansa still cikin bassinet din. Ya sake juyawa ga haisam dai. "Three?" "Yes." Haisam din ya amsa masa yana hade gira,don yasan halin Amjad da b'allo magana. "Three actual babies?" Haisam ya kalle shi. (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) "Do they look imaginary to you?" Dariya ta kaure a dakin. Har da haisam din,har Amjad dinma da saboda dariya sai daya dafa kujerar kusa dashi. "Bance haka ba.....amma sun shammaceni ne. Kasan naje Amsterdam.....daga can na biyo flight muka hadu da naseeb,basu gayan triple bane wallahi.....amma dai" Sai ya tsaya yana duban fuskokin sauran. "Nikam daga yau na sallama.....you're a true hero.....a shekara daya three babies?.....congratulations to us" Ya fada yana miqawa haisam hannu Haisam ya kalli hannun da amjad ya miqa masa,sai ya sauke idanunsa kan jariran,sannan ya dawo da kallonsa kan Omar. "Congratulations to us?" Ya maimaita cikin nutsuwa. Duka dakin ya fashe da dariya. Amjad kuwa bai janye hannunsa ba. "Of course, us." Ya amsa da cikakken qarfin hali. "Ka manta shekaru nawa muke tare? Wannan nasara ce ta qungiya." Ya fada yana shan mur saidai yanayin tsokana a fuskarsa yana nunawa sosai. Khadeem ya ballawa amjad harara sannan ya yi qwafa. "Ka ji dan rainin wayo ko." Amjad din ya nuna shi da yatsa. "Kai ka yi shiru kawai. Kai ko cat ba zaka iya raino ba." Akhnan ta kasa hana kanta dariya,don bata taba ganin wannan game din nasu har haka ba irin yau. Dole ba yadda haisam zaiyi da halin Amjad,a qarshe ya miqa masa hannu suka yi musabahar. "Thank you." Haisam din yace. Amjad ya dan tsaya,saboda ba kasafai Haisam yake fadin irin wannan kalmar ba. Ya sani,tunda ya fadi masa hakan zasu hadu ne a gaba. Amma ya maze yana boye dariyarsa. "You're welcome." Ya amsa masa. "Wallahi da gaske har yanzu ban gama yarda ba." Omar ya fada yana duban haisam. Ya nuna na ukun. "Wannan fa daga ina ya fito?" Nan take nurses din da suka shigo don ajiye sauran magungunan akhnan suka saki dariya. Kunya ta kama akhnan ta rufe fuskarta da tafin hannunta saboda dariya. Kau da kai haisam yayi gefe yana cije lips dinsa. Wato sun shirya cakar dashi ne kawai,tunda yaqi basu fuska suci namansa yadda sukeso sanda ya dauke akhnan suna yawon qasashe. Sunyi timing masa tsiyar da Allah ne yasan iyakarta,amma ya hana musu fuska,shine duka suka tattare zasu fanshe a yanzu. Dama ya sani,tunda sukayi shock sanda yace musu triple yasan yau sai yasha maganin ciwon kai saboda iskancinsu. Omar kuwa ci gaba yayi hankalinsa kwance yana tsaye kusa da bassinet din ya kasa matsawa,hannunsa riqe da qugunsa. "Ni da Naseeb har mun yi lissafi a hanya."Ya nuna Haisam. "Shi yana shirin twins." Sai ya nuna bassinets din. "Allah kuma Ya ce,qara masa daya." Dariya ta sake tashi a dakin. Har Haisam sai da ya girgiza kai wannan karon. Da gaske majanuni suke son maidashi. "You're impossible." Omar ya daga kafadunsa. "A'a, kai ne impossible ai." Sai ya kalli Akhnan cikin girmamawa. "Princess, Allah Ya saka miki da alkhairi." Muryarsa ta yi laushi a wannan karon. "Kin yi babban aiki." Ya furta har cikin zuciyarsa kuma yana ji da ganin girma da wahalar data dauka. Yara kyawawa haka manya dasu ba mitsi mitsi ba har uku a cikin dan adam. Akhnan ta yi murmushi. "Nagode." Sai Omar ya kalli haisam Idanunsa cike da fara'a. "Amma kasan wani abu?" Haisam ya daga gira don yasan tabbas ba abu me muhimmanci omar zai fada ba. "Me?" Ya tambaya yana daga girarsa guda daya. Sai Omar ya nuna bassinets din uku . "Daga yau baccinka ya qare." A wannan karon har sai da akhnan ta riqe cikinta,comedy din da suke yau a gabanta yayi yawa,bata taba ganin wannan other side din nasu ba sai yau. A nutse haisam ya kalli jariran na wasu daqiqu. Murmushi mai laushi ya bayyana a gefen bakinsa. "Dama can ba na samun isasshen bacci." "Excellent." Omar ya amsa nan take har da dan buga hannunsa kadan. "To yanzu kuma ka yi bankwana da sauran kadan din da yake saura." Dariya suka sake cika dakin,kowa yasan gari banza ma omar da haisam idan wani abu ya hadasu. Yayin da Akhnan ke kallonsu,a karo na farko cikin kwanaki masu yawa...ta ga Haisam yana dariya,wata nutsatsiyar dariya data qara masa kyau na musamman ta fidda haibarsa. Farincikin da take gani saman fuskarsa kuma kadai ya sa zuciyarta ta cika da wani irin farin ciki me ratsa zuciya. *zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 08187255862 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 08187255862 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 154* _________________________ https://chat.whatsapp.com/BkfPzSEDhnsIwyCD8LNGkm?s=cl&p=a&mlu=0 *IDAN KINSAN BA ORDER DIN KAYA ZAKI DINGA SAKAWA BA* *IDAN KINSAN BA BUSINESS KIKE DA NIYYAN YI NA KAWO KAYA DAGA CHINA BA KARKI SHIGA* *_DON ALLAH KARKI BATAWA KANKI LOKACI_* *_Assalamu alaikum my loyal people_* *_Barkanmu da wannan lokaci,kuma barkanmu da warhaka_* *_akwai da dama cikin mata wadanda suke sha'awar yin order kaya daga CHINA zuwa NIGERIA,NIJER,CAMERON,CHAD da GHANA_* *_Amma rashin samun amintaccen company....ko hannun wanda zasu dinga siyan kaya ta hannunsu cikin aminci ya hanasu_* *_To a yau addu'ar da yawa daga cikinku ta amsu,don nayo muku tsarabar kamfanin da zakuyi siyayya ta hannunsu su kuma dora muku kayanku har qasarku cikin aminci ba tare da fargaba ko d'ar d'ar ba_* *_kunsan komai nawa TASTED AND TRUSTED ne,to wannan kamfanin idan akwai abinda yafi TASTED AND TRUSTED ma shine_* *_Baki da fargaba kota sisin kwabo,ni SAFIYYA HUGUMA na tabbatar da hakan_* *_Zaki iya kasancewa dasu group nasu,inda a nan zaki hadu da agent dinsu da CEO nasu gaba daya ta wannan link din,zaki samu bayanansu da komai da ya shafi mu'amala dasu_* *INA ME BAKU TABBACIN AMINCI DA INGANCI DA SAUQIN MU'AMALA DASU DA IZININ ALLAH,BAN TALLATA MUKU SU BA SAI DANA GWADA* *Allah ya dafa mana,yasa mana albarka a nemanmu,ya albarkaci halal dinmu ameen summa ameen* _________________________ "Enough omar......nifa zargina da kake bani nakashe zomon ba....duka wannan dai kana fushi ne.....wai na raba mata na hanaka,naci amanarka.....bayan tare muka zauna a agadez....ba wanda na bawa mata.....kowa Idanunsa yakai kai ya zaba.....abeg ka barni na huta hakanan". Dariya suka sake sawa,don kowa yasan tushen matsalar dama. Qeya omar din ya juya masa,ya zaro wayarsa yana dannawa yana neman driver dinsa yace masa ya shigo da saqon da suka taho dasu. "Tunda sun qare ai shikenan.....sai ka bani saamee ai ko?" Shuru ya gilma a dakin na sakanni,kamar wani hadin baki. Akhnan ta zubawa haisam din idanu,kallon da ya jishi tar a jikinsa kamar tana gabansa ne ba'a gefansa ba. "Ko ba zaka bani ba?" Omar ya sake fada yana kara wayarsa a kunne gami da maida Idanunsa kan haisam din. Amsarsa kawai akhnan dinma take jira,ta tattara dukka nutsuwarta tana jiran jin me zaice,duk da ta nuna kamar hankalinta baya tare da su. "Inda ina da abinda zan saka maka dashi omar sama da haka da nayi. Na dade ina wannan tunanin,amma ban gaya maka ba. Tana da qualities din da kakeso tabbas......kuma na baka ita halak malak......da da sadaki a jikinka ma.....zan iya daura auren yanzun nan" Sake kwashewa sukayi da dariya har omar din daya sauke wayar a kunnensa bayan ya gama fadin saqon. "Na gode babban yaya.....zanso hakan,amma bada irin wannan gaggawar ba a satin nan zan nema ganin ta naji ra'ayinta,nima ya kamata na shiga cikinku na huta da kallon banza. Kaga wancan dan rainin hankalin ma giyar angonci yasha tazo masa har wuya ko cikakken magana baya iyayi a cikin mu...we lost him shima.....ya tafi" Ya fada yana nuna khadeem. Dariya khadeem din yake amma ya ballawa omar harara. "Ka shiga taitayinka dani....ni idan kace zaka shiga gonata zagewa zanyi mu daku" "Eh zaka iya....gwara nayi hanzarin kame kaina a nema min auren nan na shiga daga ciki ko kimata zata dadu" Ya fada yana shafa sajensa da wani irin seriousness na tsokana,suka sake saka dariya duka,daidai sanda akayi knocking dakin. Daya da daya aka shiga da wasu ledoji messengers na asibitin sannan suka juya suka fice. Omar ya tako ya dawo gaban ledar ya zauna yana budawa. "By the way....." Ya fasi yana fiddo wani elegant black box. "We didn't come empty handed". Hade gira haisam yayi yana duban omar. " Omar" Ya kira sunansa. "What?" Shima omar din ya tambaya yana hade gira. "Don't" Haisam ya fada da husky voice din nan nashi. "too late" Omar ya fadi yana dauke kai daga kallon haisam din. Tura box din yayi gaban akhnan yana cewa. "For the first prince...." Yayi maganan yana tura mata wasu rufaffun kuma guda biyu. Ido ta bude tana kallon akwatin,wani irin lafiyayyen luxury watch ne me azabar tsada da akayi da design na sarauta a jiki. Tadan fidda ido tana duban haisam da mamaki,sai ya girgiza mata kai kaman yana gaya mata. "Kadan daga aikinsu ne" "Omar" Ta kirashi saboda tasan qirar agogon,dollars ne masu yawa duk daya yake lashewa kafin a qerashi,yanzun kuma ga wasu biyun har wannan uku kenan. "No....it's an investment" Ya fada yana gyada kai da murmushi. Kafin tace komai maleek yayi magana. "My turn" Ya fada yana daukan jaka daya. Shima dai box ne,ko daya bude saiga wasu qananun gold coins da aka yiwa engraving da ranar haihuwarsu. Haisam dake tsaye kawai tun dazun goye da hannayensa yana kallon irin karamcin abokai.....aminai kuma 'yan uwa,sai daya motsa labbansa da nutsuwarnan tasa. "Maleek....wanna fa aik....." "Don't mention it please prince" Ya fada yana dan dukan kafadarsa kadan. (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) "Falaak aka bani fa....akwai wani abu da zaikai darajarta a duniya?" Maganan daya rufe bakin haisam kenan,har sanda amjad ya dauki tasa jakar Yana budewa yace. "I bought something useful....." Ya qarasa maganan yana cirowa. Wasu set din litattafai ne masu daraja,wadanda yana fiddasu haisam ya gaza ci gaba da tsaiwa yakai kansa gaban Amjad yasa hannu yana karbarsu murmushi na wadatar fuskarsa "For new borns?" "For their father" Haisam ya amsa tambayar da kansa. "Ya akayi ka samesu?" Ya tambayi Amjad yana dubansa bayan ya gama bude pages din ya tabbatar sune. Murmushi Amjad ya sauke. "Na dade da samunsu,tun last month,na killacesu ne sai rana irin wannan sannan na baka" Runguma ya kaiwa Amjad. "Na gode Amjad,na gode sosai" Murmushi can qasa akhnan tayi,a duniya ba abinda ke burge haisam irin kyautar litattafan addini. Batasan kuma inda zai kaisu ba. Library dinsa cike take da tarin litattafai tun daga sama har qasa,daga bango zuwa bango,amma har yanzu zuba wasu yakeyi. "Mine is simple" Mutallab ya fada yana ajiye envelope a gabanta. "Three trust funds.....one for each prince" "You're ridiculous" Haisam ya fada murmushi yana fadada akan fuskarsa. "We learned from you" Sai sannan naseeb ya ajiye wayarsa yana murmushi. "I brought the best gift" Ya fada da tsokana a muryarsa. Take kuwa ya kunna omar "Impossible" Ya fada yana kad'a yatsansa. "Very possible" Ya fada yana murmushi me sauti. Wata takarda ya miqawa haisam sannan ya amsa alamar ya miqawa akhnan din. "Mene wannan?"ta tambaya tana juya takardar a hannunta. "A signed agreement " "For what?" Ta tambaya a hankali tana murmushi. "Idan haisam ya zama too strict..." Sai ya nuna kansa. "I'm officially their favourite uncle" Dariya suka saki duka,sai kuma ya miqa wani wooden box. Ta bude a hankali. Azurfofi ne masu daraja a ciki,wanda aka rubuta sunayensu a jiki amma yayi sealing gurin sunan da alama ba'a shirya ta gani ba. Tayi shuru tana juyasu kyansu da qyallinau da iri tsarin da aka musu na daukan hankalinta. "Mun gode.....mun gode sasai" Ta furta muryarta na rawa,tana ganin irin tarin alkhairin dake tattare da haihuwa. Bawai don sun rasa komai ba....amma gift saboda farinciki ya samu mutum ba qaramin alkhairi bane daga ubangiji. "One day.....they'll know how loved they're before they could even speak" Idanunta taji sun cika da hawaye,saidai ko data maida dubanta ga haisam din shima su yake kalla. Nasa idanun sunyi rau rau,ya taka a hankali ya bisu daya bayan daya yayi hugging nasu bakinsa na furta kalmar. "Thanks.....na gode...na gode sosai" "Don't mind it please" Kusan duka haka suke fada sun dan bubbuga bayanshi. Ya dawo da baya ya tsaya a hankali yana qoqarin controlling emotion dinsa. "Anyway....." Omar ya fada da madaukakin sauti. "Anyway" Khadeem ma ya fada. "When are you having the fourth?" Dole ya bawa dukkaninsu dariya,haisam ya gimtse tasa yana dubansa,kafin ya nuna qofa yana fadin . "Out" Dariya ta sake mamaye dakin,wata irin dariya dake cike da nutsuwa ba hayaniya sam a ciki. Sun tafi da alqawarin shehnaz da aisa din duka zasuzo suna,kuma kwana zasuyi,magana data mata dadi sosai,har taji jiran kwanakin kawai takeyi. A wannan ranar akhnan ta fahimci cewa....yaranta basuzo cikin iyali kawai ba.....sunzo cikin wani babban da'irar mutane da suka riga suka shirya sonsu tun kafin susan sunayensu.....tun kafin susan kansu. Kyaututtukan su maleek sai ya zamana kamar bude qofa kawai sukayi.....don kafin subar asibitin wanda sukayi kwana biyar saida haisam ya hana shiga ganinsu,sai kebantattun mutane kawai. Wasu irin kyautuka ta dinga samu naban girma,wasu ma batasan su waye suka aiko da ita ba. Cikin kyautukan harda minister Agaichata Wadda ta aiko da set uku na akwati na kayan babies 'yan gaske. Sai wani handmade memory chest da zata iya ajiyar komai daya shafi yaran idan mamarsu naso. Domin adana tarihinsu da kaman kayan farko da aka fara saka musu. Hoton farko da aka fara yi musu,da sauran abubuwansu na farko da aka fara musu amfani dashi. Da kanta tayi tattaki tazo,duk da an aike mata itama da katin gayyatar bikin suna da za'ayi sati biyu da haihuwar yaran. "Nasan watarana zaki bude wannan.....ki tuna ranar da kika zama uwa" Agaichata ta fada tana murmushi hannunta akan handmade memory chest din,wanda ita kanta akhnan din ya bala'in burgeta ya tafi da ita. *NAMING CEREMONY DAY* Rana ce ta musamman......ta musamman din data adanawa akhnan wani tarihi babba cikin dukkan abubuwan da takejin ba zata taba mantawa dasu a rayuwarta ba. Ba ga iya gidan sarautar aba jifar kawai ba....aah,gaba daya jimma ce ta motsa. Jimma ce tayi wani motsi da ranar bikin sunan 'yan ukun jikokin masarautar aba jifar,sannan jinin masarautar gumma asalin salsalar yunnus jallata!. Tun ana ya gobe sunan yanayin garin ya sauya gaba daya. Akwai baqi manya mahalarta da suka dinga shigowa saboda halartar bikin. Masu iko mulki da madafun iko daban daban daga qasashe da garuruwa daban daban. Abun yaso ya girgiza akhnan,ya sake nuna mata kuma irin kyakkyawar alaqar da haisam ke da ita da mutane masu matsayi da madafan iko dama wadanda basa dashi. Agadez cif take gani a jimma,don kusan kowa da take buqatar yazo yazo din. Falaak,hairaan,nannie,shehnaz,morsa safiyya dama wasu daga cikin ahalin diory hamani yan uwan mahaifiyarta kenan. Ranar da suka iso jimma gaba daya rasa gane kanta tayi saboda murna da farinciki. Tana tsakiyarsu ana hira irin wadda ta shafi 'yan uwan da alaqa me kyau me qarfi ta shiga tsakaninsu. Shehnaz an wani sake nutsuwa,dukkaninsu ita da aisa din idan ka kallesu zakasan khadeem da mutallab sun iya riqo. Hakanan dazun da rumaisa ta shigo tayita tsokanarta,don sosai agadez ta karbeta,ta sake wani girma ta zama babbar mace sosai. Anaani kam dama kusan da ita aketa zirga zirgar haihuwar tunda ita 'yar qasa ce. Ita dinma wata nutsuwa tazo mata sosai,tana jin balqees na fadin. *zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 08187255862 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 08187255862 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 155* _________________________ *_Amintaccen gurin siyayya_* *_ingantattun kaya akan ingantaccen farashin da ba irinsa a kasuwa_* *_BONONZA DA PROMO akai akai_* *dukka sai a HUGUMA CLOSET* *Duniyar kayan yara,mata,maza,dukka* *shaddodi,atamfofi,laces,abayas,jakankuna,takalma,agogo,sarqoqi,English wears,night wears,under wears,da duk wani nau'in sutura babba da qarami* *_Karki yadda ayi babu ke.....leqa kiga yadda closet din HUGUMA kullum ke cike da kaya akan farashi me kama da KYAUTA_* *_YAN SARI....YAN REPOSTING.....DA SARAKAN ADO MASU SIYA DON KANSU....DUKKA INA MUKU MARABA_*🤝🤝🤝🤝 https://chat.whatsapp.com/FrqgC0YmUWP4FPmUzYuLJX __________________________ "Dama akwai ranar da zaki daina shegen rawar kai Aanani?" Bata amsa mata ba,sai murmushi kawai data saki cikin jin kunya. Kayan da morsa safiyya ta kawo mata ko zata buqata take budewa,abinda yafi jan hankalinta daddadan turaren shuwa incense and more daya sanyata lumshe idanunta. +234 704 229 3387. Bata iya daurewa qamshin ba,sai data kira birra tace ta dauki dukka night wear dinta ta mata kabbasarsu. "Matar nan bala'ice a turare,raina kama kaga gayya kenan,saika turara sannan zaka fahimci inda maganar take" Hairaan ta fada tana juya kwalba daya. "Shi yasa duk sanda na samu chance,ko bame zuwa nake saka order akaimin airport zuwa gumma" Falaak ta fada tana shinshina wani body milk dake cikin set din turarukan. "Inajin na fiku sanin muhimmamcin turaren nan" Akhnan ta fada wadda hannunta da yasha wani irin jan lalle ke ajiye saman bayan daya daga cikin jaririn data gama shayarwa yanzun tana so yayi bacci. Hada idanu sukayi da falaak,ita tasan dawan garin,don haka murmushi kawai suka sakarwa juna. Shigowar muhammad da sultane ahmad almaz shine abinda ya qarawa hirar armashi. Dukkaninsu a nan zasu kwana,gobe ayi walima dasu su wuce. Shikam ahmad ma sultane ne ya riqe masa agadez din kafin ya dawo,koda yazo nan sai ya ajiye sarautar ya koma ahmad dinsa sak. Hira suke sosai,yana basu labarin zamansa a Ethiopia wanda mammina ta tailasta masa zama dan qasar tun yana yaro ba tare da zabinsa ko kasan ba. Wani guri suyi dariya.....wani guri su dakata dukkansu saboda jimami. Ganin zaman labarin zai tabasu morsa safiyya ta yankeshi ta hanyar fadin. "Nikam kwanciya zanje nayi,don idan na zauna bazan samu zama hira da 'yar uwata ba bayan sallar asuba(nanay wadda bata jima da fita daga gurinsu ba). Amma saidai kafin takai ga miqewar qamshinsa ya fara yiwa parlor din maraba. Sau daya tak taja iska zuciya kwanya da kuma gangar jikinta suka gaya mata HAISAM ne. Ta lumshe idanunta tana jin yadda zuciyarta raje harbawa da qaunarsa. Missing dinsa da tayi tun safe yana saukowa ya lullubeta. A nutse yake takowa kamar baya karance da kowa a parlor din,saidai dukkan wata jijiya ta jikinsa dake harba jini zuwa zuciyarsa tana gaya masa akhnan.....da yaransa da suka kasance duniyarsa suna gurin. Ta janye idanunta a hankali sanda yake isowa gaban morsa safiyya daketa maraba dashi,yayi wani irin sassanyan kyau cikin Moroccan jallabiyya dake jikinsa dark green sosai data fidda asalin lafiyayyar fatarsa. "Barka da dare" Ya fada cikin girmamawa yana zama sosai gami da gaidata ita da nannie. Cikin kulawa morsa ta amsa.....nannie kuma cikin surukuta,don suna gama gaisawa ma ta miqe ta fara yin gaba. Hannu ya bawa muhammad da sultane ahmad suka gaisa. Wani girma suke bashi dukkaninsu,kowanensu idan ya kalleshi makomar rayuwarsa yake kalla a jikin haisam din. Allah ne ya qwacesu....haisam din shine sila. "Yaya gajiyar tafiya?" Yace da morsa safiyya yana maida hankalinsa kanta. "Alhamdulillah." Ta yi murmushi,duk sanda ta tuna d'an khaddu dinta Allah ya hada aure da diyar safeena tana jin duk duniya ba abinda yakai mata wannan nishadin a rayuwa. Tana kuma sake girmama hukuncin Allah da alqawarinsa da baya tashi idan ya tsara hakan. "Amma ba ni ka zo dubawa ba." Morsa safiyya ta fada cikin 'yar tsokana da tsakanin uwa da d'anta. Murmushi ya saki a nutse yana shafa lallausar sumarsa,sannan ya saci kallon akhnan din da wani yanayi na qwarewa,don ya kasa jurewa ya basar da ita din. Dariyar ahmad da muhammad ta tashi,haisam ya yi kamar bai ji ba. Amma idanunsa sun riga sun sauka kan Akhnan. Itama tayi kaman bata lura ba,don tasan kadan shehnaz da aisa ke jira tayi misbehaving su samu na tsokana. Sai ta zarce da gyara blanket din daya daga cikin yaran. Motsi ya fara yi,alamun yunwa ce ta tasheshi. "Feeder dinsa yana bedroom." Ta fada tana miqewa da yaron a kafadarta tana takawa a hankali. So take ta gujewa idanun haisam daketa hukuntata da idanuwansa masu nauyin miqewa morsa safiyya tayi abinta,dom ta gama karantar abinda ya shigo dashi. Matarsa ce,kuma tasan idan tana gurin zaiji nauyinta ba lallai yayi abinda ya kawoshin a zahirance ba. "Sai da safenku" Ta fada,kusan a tare suka furta "Mu kwana lafiya.....Allah ya tashemu lafiya". Kaman hakan yake jira kuwa ya miqe a nutse,ya zube hannuwansa a aljihun rigarsa ya soma wucewa zuwa bedroom din. Da idanu suka dinga gulmarsa har ya bacewa ganinsu. Wani qaramin ihu suka saki suna dariya. Zai wahala ka zauna kusa da rayuwar haisam da akhnan baka raina kalar taka soyayyar ba.. Yana da wahala ka zauna tare dasu irin kulawa da soyayyar da suke nunawa juna da wadda ke cikin idanunsu bata burgeka ba. Tana cikin dakin tana neman feeder a drawer. Duk da fiye da rabin hankalinta yana parlor din inda haisam din yake. Ba ta lura da shigowarsa ba. Sai kawai ta ji an rufe qofar a hankali. Da sauri ta waigo,idaunta cikin nasa. Sunyi wani irin laushi idanun nasa....sun rusuna sosai da yanayi na gajiya sosai a tattare dashi. "Haisamm" Ta kirashi da yanayin da tasan yana kewa. Ya tsaya cak kawai,ya jingine da qofar,hannuwansa a hade a qirjinsa,fuskarsa a nutse da wannan nutsuwar tasa.....amma idanunsa qunshe suke da wani irin kallo. (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) Ta masa kyau ainun,fatarta glowing kawai takeyi,ta dan cika kadan irin ta masu jego,saidai qiba tayi ba. Ta murmure sosai,qirjinta ya cika fam ya zauna daidai da shape din jikinta. Wannna cikin ya shafe ya koma cikin sati biyun,abun har mamaki ya dinga bashi,shape dintan nan ya fito. Fatar cikin ta batabar wani alamu me yawa ba,saboda wani hadi da nanay tayi mata traditionally daya batar da duk wani tattarewa da fatar cikin tayi ta kuma taimaka wajen fidda shape dinta sosai. "Na zo in ga ko kina tuna cewa kina da miji." Ya fada da gajiyayyar muryarsa. Kasa riqe murmushinta tayi sam. "Ta yaya zan manta da rabin zuciyata?" "Da kyau." Haisam ya fada yana lumshe idanunsa. "Me ya hanaki nema na?" Ya fada da tuhuma sosai a muryarsa. "Family dina ne fa suka zo." "Na gani." "Sun zo daga nesa." "Na sani." "To me na yi?" Ta fada a shagwabe tana dan buga qafarta kadan a qasa. Hakan da tayi kaman ta tsokanoshi ne,sai ya matso kadan. "Kin yi yini baki zo inda nake ba." "Haisam..." Ta kirashi a narke. "Kin yi breakfast tare da su." Ya daga yatsa yana irga mata. "Lunch tare da su." Ya daga wani. "Dinner tare da su." Sai ya girgiza kai. "Ni kuma?" Ya fada kaman zai sake mata kuka. Sosai ya bata dariya. "Ka girma sosai fa da za ka yi wannan rigimar....yara uku captain obbo.....amma ba zaka daina rigima ba?." "Ba ni da matsala da hakan......har abada a wajen matata......a wajen mamana ni yaro ne" Ta rufe baki tana dariya,don da alama da gaske yake. "Me kake so yanzu?" Sai ya nuna parlour din da kansa. "Ina so ki hada kayanki." "Me?" Ta tambaya da mamaki don nufinta tazo kenan sai gobe a yadda ta tsara,har tasa birra ta kawo kayansu bedroom din. "Ke da yaran." "Haisam!" Ta sake kiransa,ba tare daya danu ba yaci gaba da magana. "Zamu koma bangarenmu." "Yanzu?" "Eh....yanzu." "Family dina fa?" "Za su ganki gobe a suna." Ya fada yana sauke idanunsa akan lallenta,yadda ya zanu akan yatsunta da farar fatarta. Ya fidda kyawun siraran zara zaran yatsun hannunta. Ya saki wata boyayyar ajiyar zuciya yana jin komai nata yana tafiya da zuciyarsa da nutsuwarsa. "Amma yau..." Ya kalleta kai tsaye,abinda ya sanya ta kasa qarasa maganan. "...ina son matata da yarana." Yadda ya fadi maganan ta sani daga qasan zuciyarsa ya fito,sai ta ji zuciyarta ta yi laushi. "Ka yi missing dina ne?" Ta tambayeshi tana miqa masa hannayenta,bai bata lokaci ba ya bata nashi ta sarqesu tsakiyar nata,dumin yatsun nata suka ratsashi. Ya daga gira. "A'a." Ya fadi ,ta yi dariya ganin zai mata gatse. "Da gaske?" "Akhnan." Ya kirata a tausashe,saboda ji yayi ba abinda yake buqata irin ya rungumeta a jikinsa.. "Na'am?" "Five minutes." "Ko?" "Ko zan shigo parlour in sanar da kowa cewa kina sakaci da mijinki." Ya fada yana matsa hannuwanta da adon lallen keta burgeshi. A wannan karon ta fashe da dariya gaba daya. "An gama ranka ya dade" Ta fada tana zame hannunta da sauri tana fara shirya kayan yaran. "Baki tambayi wanne suna aka basu ba har yau" Bata kalleshi ba ta amsa masa. "Sun haifu daga uba me tarin ilimin addinu,ko wanne irin suna zaya basu....na tabbatar me ma'ana ne....kowanne irin suna zaya basu kuma.....na tabbatar zai zama mafi kyawun suna da zasuyi alfahari dashi" Alfaharin data furta shi ya mamayeshi game da ita,yaji bazai iya jurewa ba,ya taka a hankali ya isa bayanta ya mata wata kyakkyawar runguma. "Madalla da mace ta gari....." Murmushi ta saki,sannan a hankali ya dora kansa saman kafadarta. Jego takeyi.....amma wani daddadan qamshi take fitarwa da ya sanyashi lumshe ido na shiri. "Hassan......ibraheem muhammad haisam aba jifar......hussain......muhammad muhammad haisam aba jifar.......gambo.......mahmud,abun godiya kenan saboda qarin da muka samu akan abinda muka zata Allah ya bamu.....mahmud Muhammad haisam aba jifar" "Madalla da uba na gari.....madalla da miji na gari.....sultane na godiy....." ".....shshsh" Ya dakatar da ita sanda ta juyo tana rungumeshi tsam a jikinta gami da riqeshi sosai ta baya ta hanyar shimfida tafukan hannayenta a bayan nasa. "Ke.....kinsan abinda sultane yamin a rayuwa?.....kinsan me ya bani kuwa?" Ta girgiza kanta a hankali wanda yake kwance a qirjinsa tana murmushi idanunta a lumshe tana jin bugun zuciyarsa kai tsaye da kunnenta dake kwance a qirjin nasa. *zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 08187255862 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 08187255862 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 156* __________________________ https://chat.whatsapp.com/BkfPzSEDhnsIwyCD8LNGkm?s=cl&p=a&mlu=0 *IDAN KINSAN BA ORDER DIN KAYA ZAKI DINGA SAKAWA BA* *IDAN KINSAN BA BUSINESS KIKE DA NIYYAN YI NA KAWO KAYA DAGA CHINA BA KARKI SHIGA* *_DON ALLAH KARKI BATAWA KANKI LOKACI_* *_Assalamu alaikum my loyal people_* *_Barkanmu da wannan lokaci,kuma barkanmu da warhaka_* *_akwai da dama cikin mata wadanda suke sha'awar yin order kaya daga CHINA zuwa NIGERIA,NIJER,CAMERON,CHAD da GHANA_* *_Amma rashin samun amintaccen company....ko hannun wanda zasu dinga siyan kaya ta hannunsu cikin aminci ya hanasu_* *_To a yau addu'ar da yawa daga cikinku ta amsu,don nayo muku tsarabar kamfanin da zakuyi siyayya ta hannunsu su kuma dora muku kayanku har qasarku cikin aminci ba tare da fargaba ko d'ar d'ar ba_* *_kunsan komai nawa TASTED AND TRUSTED ne,to wannan kamfanin idan akwai abinda yafi TASTED AND TRUSTED ma shine_* *_Baki da fargaba kota sisin kwabo,ni SAFIYYA HUGUMA na tabbatar da hakan_* *_Zaki iya kasancewa dasu group nasu,inda a nan zaki hadu da agent dinsu da CEO nasu gaba daya ta wannan link din,zaki samu bayanansu da komai da ya shafi mu'amala dasu_* *INA ME BAKU TABBACIN AMINCI DA INGANCI DA SAUQIN MU'AMALA DASU DA IZININ ALLAH,BAN TALLATA MUKU SU BA SAI DANA GWADA* *Allah ya dafa mana,yasa mana albarka a nemanmu,ya albarkaci halal dinmu ameen summa ameen* _____________________________ "Sabon ruhi ya bani.....sabuwar duniya,ya mallakamin ruhi daya.....yayi yabanya me albarka ya bani rassa uku,wa ya sani ko a gabama hudu zan samu?" Siririyar dariya ta saki tana boye fuskarta a qirjinsa. Bayan mintuna kadan kuwa...Muhammad da Ahmad dasu shehnaz dake zaune sai ganin haisam sukayi da akhnan,yana tura stroller din yarantana biye dashi a bayansa. "Ni na sani." Shehnaz ta fada qasa qasa cikin gulma. "Ni ma." Aisa ta masa tana boye murmushinta "Ya kwashe ta kenan?" Ahmad ya fada shima yana boye gulmarsa. "An gama."muhammad ha fada yana laluben Aanani dinsa a waya. Yana jin kawai gwara tazo suma su wuce. "Zan dawo da ita gobe." "Ba mu yarda ba." Ahmad ya fada yana murmushi. "Ba tambaya na yi ba." Haisam ya amsa masa yana dan jifansa da hararar wasa. Dariya sukayi cikin nishadi,ya saki qaramin murmushi suna jerawa da akhnan din suka fice daga parlor din. *WASHEGARI* Tsaftatacciyar walima ce da aka yita har kashi biyu. Daya ta kowa da kowa,saita bayan la'asar data kasance iya jini da tsatson masarautun biyu ne. Idan kaga yadda masarautar ta koma a ranar zaka dauka wani gagarumin biki akeyi na amare da angwaye goma. Ciyarwa kawai akeyi irin wadda ba'a taba irinta ba. Sadaka kawai ake fitarwa daga taskar haisam dama motii dinma gaba daya kamar zasu qarar da abinda suka mallaka. Danyen abinci kuwa ba'asan adadin tirela nawa aka qarar ba. Tufafi da kudi kuwa ba'a maganarsu. Duk da kasancewarsu masu tsananin kyauta sadaka da alheri wa talakawansu,amma wannan ranar wannan lokaci komai ya zama na daban. Cikin dakin walimar data zama ta relatives kawai. Kyautuka ne akhnan ke karba har suka sanyata ta fara qwalla. Nanay....motii....sultane,morsa safiyya.....shehnaz aisa,rumaisa.....Anaani.....balqess.....khansaaa......Areef....ga uban 'ya'ya hussam da ta kasa daina mamakin yadda yake kyauta baya tsoron talauci sam. Wata irin kyauta dake nuna zallar soyyayar da yakewa yaran kamar shine ya haifesu. Ga wani account daya bude a take wanda zai dauki dawainiyar karatun yaran daga randa suia tsoma qafa a makaranta har randa zasu kammala. Daidai da noorah wadda ita ta zama photographer a gurin tata kyautar ta wankewa akhnan kai gaba daya. Ta dinga juyata tana mamakin inda ta samu kudi irin wannan ta siya abu me tsada da daraja na kudade masu nauyi ta bawa yaran Ashraf.....asif da afeef,sune sunayen da iyayensu su shehnaz dasu rumaisa suka hadu suka zaba musu bayan sun tabbatar da ma'anar sunan me kyau ce. Ta sauke idanunta akan yaran dake kwance cikin wasu qananun royal bed dake nuna su din da gaske jini ne na sarauta.....gadon da akayi order dinsa direct daga italy,bayan yarjejeniya da kamfanin da haisam yayi dasu kan su kadai zasu siyarwa design din,aka qerashi da miliyoyin kudi kuma suka aiko dashi. Inda gata yana yawa,ta tabbatar zaiwa yaranta yawa. Inda gata yana zarce misali zatace nasu ya wuce wannan. Sai a yanzu take gane lallai ba shakka.....a baya ba wani gata gareta ba data dage tana qafafafa dashi,ga inda asalin ainihin gatan yake nan. Ta daga idanunta a hankali akan haisam daya miqe a nutse,yana takawa sanye da wasu tsaddadun jubah da cloak throbe qirar 2027 data kasance mallakarsa,kuma mutum na farko da kamfanin na al_imaraat suka saqa masa ita. Abin mamaki,yau da kansa ya isa gurin jawabi,abinda sam ba kasafai yake son yin jawabi a tarurruka na family ba. Nanay ma ta daga kai tana kallonsa. Sultane daya iso a ranar zai kuma koma zuwa dare yayi murmushi. Saboda ya san akwai wani abu. Yana iya karantar haisam daga yanayinsa kawai. "Yau ba ranar yaranmu kawai ba ce." Shiru ya mamaye wajen. "Yau kuma rana ce ta godiya." Sai ya juya ya kalli Akhnan. "Na gode wa Allah da Ya bani su." Ya fada yana sauke idanunsa akan su ashraf. "Kuma na gode wa matar da ta kawo su duniya." Akhnan ta sunkuyar da kanta cikin kunya. "Amma kamar akwai buqatar godiyar tafi haka" Akhnan ta dago kai,sai idanunsa suka dawo kanta.Kai tsaye. Ba tare da ya kau da kai ba. "Matata." Wajen ya yi shiru gaba daya. Akhnan taji wani sabon nauyin. "Mutane da yawa suna taya uba murna." Ya girgiza kai. "Amma ni na san wanda ya cancanci yabo." (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) "Na ga wahalar da ta sha." "Na ga tsoron da ta boye." "Na ga addu'o'in da take yi lokacin da babu kowa." Akhnan ta sunkuyar da kanta tana mamakin yadda ashe yake bibiye da dukka wani motsinta. Sabbin hawaye suka fara taruwa a idanunta. Da salon mulki da izzar nan ta jimma,wadda ta zama jinin jikinsa yayi alama da hannu kawai,nan take aka kawo wani velvet folder. Karba yayi,sannan kai tsaye ya miqawa akhnan. "Open it." Da mamaki ta karba da hannu biyu kaman yadda take karbar abu daga gurinsa yanzu. Ta budeta a nutse. Da farko ba ta gane ba. Sai ta sake kallon rubutun. Sannan ta sake dubawa. A saman takardar an rubuta *THE AKHNAN ESTATE* Sai hannunta ya yi sanyi. Maison akhnan ne ke dawo mata. Wannan dinma ba wata kyauta bace ta qaramin abu. Ba wani zobe bane......wani cikakken estate ne. A cikin manyan kadarorin daular haisam. Me private gardens....library.....children's wing......amily courtyard... Artificial lake.....Private masjid.....underground royal gallery,komai an tsara shi da abubuwan da takeso kaman mafarkinta ne a gabanta. "Haisam..."Ta kasa qarasawa saboda yadda jikinta yayi sanyi gaba daya. Kaman yana nuna over soyayya a kanta. Kamar wannan qaunar tayi yawa,me ta masa?,me ta bashi data cancanci wannan gaba daya?. Duruqsawa yayi sosai kusa da ita. Abin da ya sa duk wajen ya yi shiru. Saboda sabon abu ne,haisam din ba qaramin abu ne yake sanyashi fallasa zuciyarsa haka ba. "Kin bani gida." Ta kalle shi cikin mamaki. "Na yi shekaru ina da gidaje."Sai ya girgiza kai. "Amma ban taba samun home ba sai da ke." Nanay ta rufe bakinta,hawaye suka cika idanunta. Morsa Safiyya ma ta fara share hawaye a hankali. Su kansu abun wani burgesu yakeyi.....soyyayar da suka jima basuga irinta da gasken gaske a soyyayar zamanin nan ba.....a tattare da yaran zamani irinsu ba. So saboda Allah kawai,ba don ta bashi komai ba. So saboda Allah kawai.....saboda kyakykyawar mu'amalarsa ba don tasan wayeshi ba. "Na gina wannan tun kafin a haife su." Ya nuna yaran. "Saboda na san wata rana zan so in nuna miki cewa..." Sai ya dan yi shiru. "...duk abin da na mallaka zai iya qarewa." Ya furta kalmar sanda I danunta suka hadu da nasa. "Amma darajarki a wurina ba za ta taba raguwa ba." A wannan lokacin Akhnan ta kasa magana gaba daya.Ta ji kamar zuciyarta ta yi nauyi saboda soyayyarsa daya sake cusa mata da kuma wani irin launin farin ciki. "Karbi" Taji muryar nanay daga gefanta. Akhnan ta waigo a hankali tana duban uwar mijin nata. Uwar mijin da inda za'ace ta bada award na har abada ga best uwarmiji ba ko shakka nanay zata danqawa shi gaba daya. "Wallahi kin cancanta." Ta sake fada tana kallon akhnan sosai tana gyada kanta. "Fiye da haka ma." Muryar motii ta marawa ta nanay baya. "Yayi yawa" Akhnan ta fada cikin karaya,tana ganin kamar batakai girman wannan kyauta ba. "Not enough." Ya fada da dukka zuciyarsa. Akhnan ta girgiza kai itama tana duban abinda ke narkewa a idanunsa. "Haisam..." "Not enough."Ya sake maimaitawa idanunsa cikin nata. "Da zan iya biyanki saboda duk abin da kika yi..." Ya girgiza kai. "Da babu wani abu a duniya da zai isa biyanki wannan aikin.....wannan wahalar..." Nanay ta sake share hawaye tana jinjina kai gami da gamsuwa da maganganun haisam gaba daya. A hankali morsa Safiyya ta juya gefe tana murmushi zuciyarta na mata wani irin sanyi. Irin mijin da safeena ta yiwa diyarta mafarki. Shi ta samu,sama da haka ma,itakam ko yanzu ta fadi ta mutu,tabbas tana da amsar bawa safeena,zata iya tsaiwa ta fuskanceta. Matsawa yayi kusa sa ita,ya sunkuya qasa qasa ba tare da kowa yaji ba. "You're crying giiftii" "Saboda kai ne" Ta fada a shagwabe. "Good" Ya fada yana murmushi. Da mamaki ta kalleshi. "Yes" Yace yana dage girarsa. "Because now everyone can see...." "Can see what?" "How much you love me" Ya fada da zolaya fal muryarsa. Ga mamakinsa tattausan murmushi ta saki,ta rausayar da kanta gefe. "Ban fadi ba....duk irin son dana nuna maka ban fadi ba,koda a gaban waye" Ta masa surprise daya kasa magana,sai lumshe idanunsa kawai da yakeyi ya gaza daina kallonta. A wannan ranar...ba estate din kawai bane ya sa mutane da yawa taya akhnan kukan murna ba......Ba girman kyautar ba ne. Abin da ya taba zukatansu shi ne.....sheikh muhammad haisam......mutumin da ya shafe shekaru yana gina dauloli da kamfanoni....amma zabi ya sanya sunan mafi kyawun abin da ya gina da sunan Akhnan. *zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 08187255862 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 08187255862 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 157* __________________________ *_INGANTACCEN MAGANIN SANYI NE SADIDAN,WANDA BA'A CAKUDASHI DA KOMAI BA SAI ZALLAR SASSAQE DA ITATUWA MASU AMINCI_* *_KAYAN GYARA MASU INGANCI DA WARWARE MATSALAR MATA TA FUSKAR CIWON SANYI WANDA YA KASA JIN MAGANI_* *_GARZAYA A SIRRANCE KI WARWARE MATSALARKI,KI TUNTUBETA TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE_* +234 810 914 9876 ___________________________ Idan da za'a tambayeta menene rayuwa?. Zata iya cewa HAISAM ne. Idan da za'a tambayeta mene RUHI ZUCIYA MAFARKI da BURI duka zata ce haisam ne. Idan za'a tambayeta mececw SOYAYYA ko QAUNA?.....MENE FITAR NUMFASHI DA BUGAWAR ZUCIYA.. dukka zata iya cewa ASIF NE.....ASHRAF NE....AFEEF NE. Idan aka tambayeta kinsan rayuwa?. Zata ce aah,....sai a yanzu. Sai bayan da Allah ya mallaka mata haisam. Sai bayan data haifi ashraf asif da afeef sannan tasan me duniya ke nufi da RAYUWA. MUTUM HUDU dinnan.....mutane HUDU dinnan sun zama RUHINTA da batajin zata iya rayuwa ba tare dasu ba. Mutum HUDU dinnan da kullum take kwana take tashi da fargabar rasa daya daga cikin su. Mutane hudun nan da kullum take addu'a kada Allah ya jarabceta da rasa daya daga cikinsu. Wata ingantacciyar rayuwa.....wadda take kwanciya da burin ganin kamar wanzuwar rayuwa me kyau wa ahalinta. Wara rayuwa da take farkawa da sautikansu su hudun. Haisam da yaransa......ta kwanta dasu dumin jikinsu yana gogar nata. Wata rayuwa ta tsarawa kanta. Duk wata wahala ta raino ta koyawa kanta. Bata yarda da rainon hadimai ba.....bata yarda da rainon bayi ba.....bata yarda da rainon 'yan aiki ba. Tafi ganewa ta hidimta musu da kanta. Bata yarda da kowa akan yaranta ba indai ba jininsu bane. Rayuwarta a hannun mammina wata irin izina ce.....wani irin karatu ne me zaman kansa da kansa. Karatun da wataqila mammina bata mata shi ba....ba lallai ta gane ta sauqi haka ba. Silently ta dinga gyaran kanta....silently ta dinga Maida kanta macace ta hanyar koyin hanyoyin kula da miji da yara. Ta sanya dukkan hankalinta da qarfinta a kai. Yadda cikin lokaci kadan ta iya komai,....cikin qaramin lokaci ta zama cikakkiyar mace da zata iya kula da gidanta da mijinta,wannan ya gaya mata lallai komai idan mutum yaso zai iya gyara rayuwarsa. Idan mutum yaso zai iya gyara kansa...... Idan har mutum yaso zai iya gyaran kurakuransa. Ta yarda komai soyayyarki da cikarki mace...akwai abubuwan da idan baki iyasu ba....komai kawaicin da namiji zai miki kina da naqasu. Har yanzu idan tayi wani abun mamaki kashe haisam yakeyi. Yaya akayi ta iya?. (Karki saki baki waike ai ana sonki,ai shi baida damuwa don bakiyi kaza ko ba'ayi kaza ba. Komai kawaicin namiji indai baki iya wani abu da yake so ko yaya ba.....zai iya kawaicin,ya dauke kai.....amma acan cikin ran shi yanaso,yana kuma kewa,idan kuma kin iya din zaiji dadi,zaki gane hakan bayan kin iya din). Taso ya barsu taci gaba da kula da yaran,shi kuma yayi focusing akan business dinsa da boyayyen aikinsa. Amma koda ya amsa mata da to......idan tafiya ta kama,koda ya fita saidai taga ya dawo da kanshi yahau hada kayansu asharaf,saidai ta tsaya cak tana dubanshi. "Abbee" Sunan da takan kirashi yanzu kenan. "Mm" Sai ya amsa amma bazai dubeta ba,don yasan qilan qorafi ne "Amma fa....." "I'm sorry,bazan iya tafiya na barku ba,Even if I force myself to go, aikin ba zai yi min dadi ba....aikin bazai yuwu ba....ko kinason ganin faduwar mijinki?" Tana ji tana gani dole haka take rabuwa dashi. Sun zama kamar aljihunsa,duk inda ya zaije sai ya daukesu hankalinsa yake kwanciya. Akhnan ta yi murmushin nan dake qara mata kyau. "Drama prince." "No." Ya amsa cikin sanyin murya. "I'm very serious." Ta girgiza kai. Tun da yaran suka zo duniya...ta fara ganin wani sabon haisam. Wani haisam da yake saurin komawa gida. Wani Haisam da yake duba hotunan yaransa a tsakiyar meeting. Wani Haisam da baya iya yin yini bai gan su ba. "Ranan da suka shiga school,zanga yadda zamu dinga yawo dasu" Ta taba cewa dashi. Murmushi ya saki yana kallon tsakiyar qwayar idanunta. "Ba abinda zai sauya....ba abinda za'a fasa. Su dama 'yan rakiya ne ai". Akhnan ta qyalqyale da dariya. "Yan rakiya?" "Yes." "For the rest of their lives?"Sai ya kalleta,wannan kallon da kullum ke sa zuciyarta ta narke. "For the rest of mine." Na dan lokaci Akhnan ta kasa cewa komai. Saboda yadda ya fad'a. Ba wasa ba. Ba tsokana ba. Da gaske yake. A wurin Haisam...dukiyarsa..... Sarautarsa.....Kamfanoninsa.......nasarorinsa. Duk suna da matsayinsu. Amma babu abin da yake so ya dauka tare da shi kamar matarsa da qananan sarakunansa uku. Yaran suna da watanni takwas ta aurar da nata 'yan biyar din. Birra barratu buhaina bushira da baraka. Saidai kusan dukkaninsu sun aminta suci gaba da aiki da ita,don haka a cikin villa dinsu aka warewa kowa apartment daban shi da mijinsa,don masu gidan nasu ma duka 'yan gidan sarautar agadez ne,birra ce ta samu dan cikin masarautar jimma. Tana tafi da kowanne company nata daga gida ta cikin system. Sau bibbiyu bayan haihuwar su ashraf taje dubai da Niamey tayi ziyarar gani da ido ta duba duka companies din nata. Meeting.....shawarwari da gudanarwar kamfanonin daga gida takeyi. Bayan ta sallami haisam din,ta kuma sallami yaran,a kowacce rana awa uku ko biyu take warewa tana aiki saman saman system tana gudanar da komai,idan ta rufe kuma sai washegari,saidai idan wani abun ya taso su sanar mata tahau ta duba. *_BAYAN SHEKARU_* Safiyar Jimma ta kasance cikin nutsuwa. Iskar sanyi daga tsaunukan Jimma na motsa farin curtains din balcony a hankali,yayin da hasken safiya yake shiga cikin bedroom dinsu mai fadi da wani irin tsari dake bada iska me dadi da wadataccen haske. (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) Itama don dai kawai ba'a manta asali.....kuma ba'a manta gida. Amma saura qiris a lokuta da danma ta zabu jimma sama da agadez. Garin yana da wata irin albarka,hakanan yana da wani irin weather dake sanyaya zuciya. Irin weather din da yawancin zukata da gangar jiki sukeso,irin yanayin nan me sanya nishadi a zukata. Akhnan ce,tsaye bakin glass railing din tana riqe da cup din tea dinta. Ta zama wata irin mayyar tea har abbee(haisam) yana tsokanarta a gaban yara su kuma suna tayashi. "Mun maidata 'yar jimma....cikakkiyar yar Ethiopia....mun mantar da ita agadez gaba daya" Daga qasa...dariyar yara ta cika garden din. Ta sauke idanunta a kansu tana kallonsu daya bayan daya. Ba ashraf bane.....ba asif bane....ba afeef bane. A yanzun....wasu yaranne na daban.....wasu saitin 'yan ukun daban......da wani set na 'yan biyun da suka zama haihuwarta na qarshe da tayi shekaru biyu baya. Ahsan.....ahlaam......da ajmal.....sai 'yammatan da suka kasance twins su biyu masu tsananin kama da akhnan din kamar kakinsu tayi ta ajjiye. Safiyya da safeena.....wanda nanay tayi kawaici tace sunansu ya kamata ya saka ita ta yafe. (YUMNA DA YUSRA). Yumna ce ke gudu tana qoqarin kaucewa kubuta daga hannun ahsan wanda yakeso lallai sai ya riqeta kada ta fadi,yayin da nannynsu ruqayya yarinyar da bata haura shekara sha uku ba ke binsu cikin dariya. Murmushi ya bayyana a fuskar Akhnan ba tare da ta shirya ba. Years ago...... da wani ya gaya mata cewa zata taba samun irin wannan rayuwar,da bata yarda ba. Ba wannan mutumin ba...yarima sheikh Muhammad hausam. Ba wannan gidan ba......ba wannan nutsuwar ba. Mafarkinta yayi nisa akan ta rayu ita kadai kawai. Mafarkinta yayi nisa yana gaya mata lallai akwai rashin 'yanci da takura gurin rayuwa tare da d'a namiji. Ashe dai saidai ga wadda bata dace ba. D'A NAMIJI.....KUMA MALAMIN data raina.....shi ya zame mata wani tsani na kaiwa wani mataki da bata taba mafarkin kaiwa ba kaf rayuwarta. Malamin dai.....shine ya kama hannunta ya sanyata ta san ma mene addininta haqiqanin sani. Ya sanyata ta sauke litattafan addini da dama. Ya sanyata ta gyara lahirarta ta hanyar yin karatun litattafan addini masu yawan gaske daga bango zuwa bango. Ta sauke hadisai masu yawa,litattafan fiqhu dana sira. Tasan rayuwa a haqiqanin zahirinta. Tasan mutuwa hisabi da kwaciyar kabari sanin da bata taba kaiwa koda gefansa ba. Ya sanyata da kudinta da abinda ta mallaka takewa kanta mahaifiyarta da morsa safiyya sadaqatul jariya. Harda wadanda ta manta. Yawan sadaqar ya sanyata take mafarkin mahaifiyarta cikin ni'ima a mabanbatan lokuta. Allah ya nuna mata a mafarki yadda sadaqatul jariya dinta ke isa ga mamminta. (Iyayenki sun mutu?,amma kina da dubu hamsin,dubu dari da zata isa gina rijiya......siyan qur'ani kikai masallaci......gyaran hanyoyin unguwarku ko yin cikon hanya amma ki kasa yi musu wannan kice ladan Allah yakai kabarinsu?). Sharrin mammina bai hanata roqa mata yafiyar Allah ba....sharrinta bai hana mata yi mata sadaqatul jariya ba tunda bata da wanda zai mata. Tana fatan wannan ya sanya ta samu sassauci a gurin Allah. (A duk sanda bawa ya maka sharri,kai kuma idan ka samu dama akansa gwada masa alkhairi. Yi masa alkhairi har sai ya kasa kallon idanunka,Allah kasa mufi qarfin zukatanmu....kasa mu shuka alkhairi don mu girbeshi ranar gobe qiyama). Tayi nisa a tunaninta sai ta ji motsin qofa a bayanta. Ba sai ta juya ba kafin ta san shi ne. Presence dinsa har yanzu yana nan quiet power. calm danger. the same man.......prince sheikh muhammad haisam. Wannan kamannin.....wannan lallausan kyan....wannan charisma din.....haiba,kwarjini,kamala dukkansu suna nan tattare dashi,sai ya zamana kamar an ninkasu ne ma. Da tarin nutsuwar nan tasa ya tsaya bayanta cikin dark suit dinsa,ya zube hannayensa a aljihun suit din,saidai hakan bai hana bayyanar agogon hannunsa dake kyalli qarqashin hasken safiyar ranar ba. “Kika gudu kika barni da su.” ya fada a tausashe da wannan husky voice din tasa me zurfi,wadda idan yayi magana take kai mata kowanne sashe na jikinta. Ta yi murmushi tana kallon garden,har yanzu anata artabu da yumna. Kuzari tafi kowa a gidan?,ko rashin ji?,itadai ba zata ce ba. “They like you more.” ta amsa masa da muryarta dinnan da bata sauyawa “A’a.” ya fada a tausashe,sannan a nutse ya tako ya qaraso kusa da ita yana aza hannunsa jikin makarin silver din. “They fear me more.” Tayi qaramar dariya tana duban idanun nan nasa da kowacce rana yake sake narkar da ita. "Abbee....yaran nan wani lokaci abinsu baya tashi ma sai sun ganka fa" Murmushi ya saki a hankali,ya miqa hannunsa yana dan ja hancinta da yaga ya bude kadan. *zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 08187255862 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 08187255862 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 158* __________________________ *_Amintaccen gurin siyayya_* *_ingantattun kaya akan ingantaccen farashin da ba irinsa a kasuwa_* *_BONONZA DA PROMO akai akai_* *dukka sai a HUGUMA CLOSET* *Duniyar kayan yara,mata,maza,dukka* *shaddodi,atamfofi,laces,abayas,jakankuna,takalma,agogo,sarqoqi,English wears,night wears,under wears,da duk wani nau'in sutura babba da qarami* *_Karki yadda ayi babu ke.....leqa kiga yadda closet din HUGUMA kullum ke cike da kaya akan farashi me kama da KYAUTA_* *_YAN SARI....YAN REPOSTING.....DA SARAKAN ADO MASU SIYA DON KANSU....DUKKA INA MUKU MARABA_*🤝🤝🤝🤝 https://chat.whatsapp.com/FrqgC0YmUWP4FPmUzYuLJX ___________________________ Akwai shaquwa da sabo da sakewa sosai tsakaninsu sama da yadda suka sake da mamansu..... Amma akwai wani tsoro da respect a tsakaninsu. Wani shakkarsa suke....musamman idan kasan kayi ba daidai ba. Amma kuma idan kaga yadda suke rayuwa dashi zaka dauka abokinsu ne ba uba ba. "Hancina ko abbee" Ta fada taba dan tsuke fuska. Ido ya zuba mata sosai kaman bayason ya daina kallonta. Itama kallonsa take tana sake ganin yadda kyansa ke sake fitowa yana cakuda da shekaru wadanda ke sake qara masa kwarjini. Mutumin da duniya ke tsoro… ita ce kadai take jin yadda zuciyarsa take samun wata cikakkiyar nutsuwa idan yana gida. "No" Yace yana danne murmushinsa. Rau rau tayi da idanu tana dubanshi. "Kaji tsoron Allah ka fadi gaskiya" Ta fada muryarta tana raurawa kaman zata sake masa kuka,abinda ya tilasta dariyanshi fita gaba daya. Siririn kuka ta sake masa,amma kuma da gaske abun mamaki qwalla take fitarwa,ya dan zaro ido yana mamaki.....saidai kafin yace komai,sai qaramar muryar yusra ta taso daga qasa. “abbeee!" Ya sauke idanunsa sanda take rugowa qofar da zata sadata da inda suke tsayen kafin ruqayya ta kai ga kama ta. Idanunsa ya maida kan akhnan yana narke idanunsa shima. "Ki rufan asiri ammee...(sunan da yaran ke Kiran ta?,kinga dai banyi miki komai ba...hasalima yau ni aka yiwa laifi,da asuba akaqi sanmin abun arziqi. Yanzun yusra zata shigo,idan taga qwalla a idonki tace me na yiwa ammeenta?" Banda bacin rai kadan da takeji wanda batasan asalinsa ba,tabbas data qyalqyale da dariya. Saboda haisam din wani irin mutum ne da sam bayaso yaranta suga alamun ya bata ran mamansu. Ya taba bata amsa da cewa. "Inaso su taso da tausayin iyalansu suma a gaba,dole sai ina kwatantawa. Yaro kuma baya mantuwa,komai a kansa yake zama,inaso su samu memory me kyau....inaso su tashi da yiwa rayuwar aure kyakykyawan zato,adadin kulawa nutsuwa da kwanciyar hankali da kuma soyayyar da yaro ya samu,adadin yadda zai dinga mu'amala da kowa a waje. Da taushi,da nuna qauna da soyayya ga kowa,ba tare da musgunawa ba" .ta gamsu da hakan dari bisa dari,don tana ganin tasirinsa tattare da yaran. "Ba kaine ba.....dariya kakewa hancina". " Na tuba.....na tuba giiftii din jimma" Ya fada yana hade hannayensa guri daya. Daidai lokacin yusra ta iso. Yusea me sleepy eyes ta bayyana bakin qofar gurin tana kallonsu duk sy biyun. Sai dukkaninsu suka bude mata hannayensu,da gudu ta rugo,amma sai ta zabi fadawa jikin haisam. Dan ihu ya saki yana dariya wa akhnan din. Murmushi kawai ta saki,don dama tasan hakan na iya faruwa,bata sanya rai da yawa tazo gurinta ba. Dagata sama yayi yana zagaye gurin da ita yana mata wata waqar larabci da yakan rera musu tun suna jira jirai idan suna kuka. Burgeta kallonsu yakeyi......haisam.....mutum na musamman a duniya. Bata gajiya da fadin hakan. Idan ka ganshi cikin iyalinsa ba zakace shine wanda kullum manyan attajirai da manyan shuwagabannin duniya ke jiransa ba. Yadda yusra ta kwantar da kanta a kafadarsa kawai ya isa ya gaya maka ita kanta ta gamsu tana da amintaccen uba a duniya. Yadda hannun Haisam ya riqeta instinctively. Yadda cold din mutumin nan yake narkewa a gaban iyalinsa kawai,sai idanunsu suka hadu da nata. Na wani second guda… duk memories suka dawo mata. hamadar agadez,tsoron da suka fuskanta a tare,jarrabawar rayuwarsu da mammina....soyayyar da ta firgita ta. Da kuma daren da ta taba tunanin bazata iya rayuwa cikin duniyarsa ba. Yanzu kuma…ita ce duniyar tasa. Haisam ya kalleta cikin nutsuwa irin tasa muryarsa a qasa yadda yusra ba zata fahimta ba. “Why are you looking at me like that?” Ta girgiza kai a hankali. “Just thinking.” “Dangerous.”Ta yi murmushi,still him. Amma taqi bashi amsa. Ta sani tsaf zai qarar da duka lokacinsa a gurin,bayan tun a jiya tasan fitar yau me muhimmanci ce. "Zaka wuce ne?" Ta tambaya kaman me masa tuni. Ya sani.....meeting dinsa na jiransa. Phones suna ta vibrating tun safe. Duniya tana jiransa kamar kullum. Amma sai ya kalli matarsa......'Ya'yansa.....gidansa sannan calmly yace “No.” Akhnan ta dan daga idonta a kansa. “Your meeting?” “It can wait.” ya furta yana rage tazarar nisan dake tsakaninsu. Sai ya qaraso gare ta,ya tsaya kusa da ita yusra na rungume a jikinsa. A wajen balcony din… ,wata irin iska mai sanyi da dadi ke ratsasu. Garden din na cike da tsirrai dake bada iska me dadi har nan inda suke tsaye,shi yasa aka gina gurin daura da garden din. Rana mara haske da qarancin zafi tana haskaka gidan kamar wata sabywar rayuwa. A nutse haisam ya sumbaci goshin akhnan din,sai yusa ta kalleshi,ta kuma tura masa tata fuskar. Dariya suka sanya dukansu ita dashi,yayi kissing nata itama,saita qanqame wuyansa tana murna,abinda ya sake basu dariya gaba daya. "Kawota.....kaje ka dawo.....zaka samemu cikin aminci da yardar Allah". Girarsa dukka biyun ya dage. " Are you sure?" Kai ta daga masa a tausashe. Ya miqa mata yusra,amma saita maqale kafada. "Ba zata yarda ba...." "...muje na rakaka sai na karbeta a bakin motar" "Kina nufin da ba zaki rakani ba yau?" Ya tambaya yana bata fuska,ta saki murmushi kawai. Kasala take fada da ita kwanan nan duk safiya,batason gaya masa yanzun nan zai rasa nutsuwar sa,sannan uwa uba ma zarginta yafi qarfafarta akan ciki ne,don duka alamunsa sun nuna mata. Tare suke takawa da wani irin yanayi me dadi inda jerin motocinsa ke jiransa. Dab da zasu fita yaran na shigowa. Dukkaninsu suna maqaleshi,hakanan ya sunkuya ya dauki yumna itama,su ahsan suka riqeshi ta gefe da gefe suna zuba masa surutu,duk da yadda akhnan ke fadin kada su bata masa kaya sam bai damu ba,don pyjamas ne duk a jikinsu,yau ba wanda yayi wankan safe,sannan duk yashin gefan pool na gurin ya bata hannuwansu da qafafunsu. Akhnan na kallonsu tana girgiza kai. Wannan abu na yaran idan haisam zai fita bai taba canzawa ba. Ko da yaushe sai sun yi masa rakiya,indai suna gidan,indai idanunsu biyu. "Abbee,ka kalli kayanka." Akhnan ta fada sanda daya daga cikin amintattun guard dinsa ya bude masa qofar motar ya kuma zura jikinsa. Ta nuna farin shirt dinsa da yanzu yatsun yumna suka bar masa alamar yashi. "Meeting zaka je fa." Sai ya kalli rigar. Sannan ya kalli yaran. "So?" Ya furta yana dage mata dukka girarsa. (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) "So?" Ta maimaita tana dariya. "Ba su ne suka bata min ba." Ya fada yana kade gurin da wani dan farin handkerchief me kyan gaske da guard dinsa ya miqa masa a girmame. Ajiyeshi yayi,ya sake jawo yumna da yusra ya dan rungume su. Ya miqa musu kuncinsa,sai kowacce ta bashi kiss guda daya. "Sun qara mata kyau ma rigar." Dariya ta kubce mata daidai sanda Yumna ta sa qananan hannayenta biyu ta riqe fuskarsa. "Abbee..." "Na'am, princess?" Ya amsa yana shafa sassalkar sumarta me tsaho da santsi data gada daga buzuwar babarta. "Kar ka dade." Nan take zuciyar Akhnan ta yi wani irin laushi. Yarinyar nada wani irin wayo na daban,har yanzu idan zai tafi sai sun gaya masa hakan. Sunkuyo da kansa yayi ya sumbaci goshinta. "I won't." "You said that yesterday." Ahsan ya fada,akhnan ta rufe bakinta tana dariya. Da dariya a fuskar haisam ya juya ya kalli ahsan. "Whose side are you on?" "Mama's." Ya fada yana tsalle da dariya. "Me too." Ajmal ma ya fada yana dariya. "Me three." Yumna ma ta fadi tana daga yatsunta uku duk da bata gama fahimtar akan abinda ake maganar ba. Sai kawai ya girgiza kai kamar wanda aka ci nasara a kansa a yaqi. "Traitors." Yaran suka fashe da dariya. Dariyar itama ta danyi,saidai kuma ta ji wani jiri sama sama ya ratsa ta. Ta dafe gefen motar a hankali tana kiran sunan Allah. Ba wanda ya lura sai haisam. Nan take murmushinsa ya dusashe. "Akhnan." Kirata da kulawa. Ta dago kanta a nutse. "Hmm?" Idanunsa suka tsaya a kanta. Na dan lokaci kamar yana qoqarin karanta wani abu. "Are you alright?" "Of course." Ta amsa masa da confidence. "You're tired." Yace yana zare seat belt dinsa da sauri. "Just a little." Ta fadi tana daga masa hannu gami da dakatar dashi,saboda ta fuskanci fitowa yakeso yayi,kuma taga yadda hussam keta kiransa,da alama abune me muhimmanci. Dakatawar yayi amma sai ya ci gaba da kallonta kamar bai nutsu da yanayinta ba. Wancan kallon dake mata nauyi,don idan ya fara yi mata shi.....yana ganin abubuwan da take son boyewa fes cikin idanunta. "Kinci abinci?" Ya sake tambaya. "Eh naci,ka shigo ka ganni da cup ba?" "Properly?" "Muhammad." Ta fada tana yarfe hannunta kamar yarinya irinsu yumna. "Akhnan." Ya kirata shima don bazaije ko ina ba sai ya tabbatar lafiyarta qalau. Yaran suka fara kallon iyayensu. Saboda sun san wannan yanayin. Tsananin kulawa da junansu da baya boyuwa ko a gaban waye. Haisam ya ci gaba da kallonta,sai kuma ya sauke ajiyar zuciya. "Rest today." Ya fada daga qarshe. "I will." Ta amsa masa. "Banda shiga kitchen yau duka.....ba girki na auroki kiyimin ba" Qaramin murmushin da bata shirya ba ya qwace mata. Dole sunan NA MUSAMMAN batasan sanda zata sauke masa shi ba. Abubuwan da maza da yawa suka daukakesu,suka kuma daukesu da zafi shi basu dameshi ba. Kawai shi ta zamana cikin qoshin lafiya,ta kula da tarbiyyar yara,sannan ta kula da buqatunsa a shimfida,komai ba dole bane a wajensa idan ya wuce wadannan. "Promise?" Ya tambayeta. Sai ta gyada kai. "Take care of yourself......" Yayi maganan yana miqa mata hannunsa kaman yadda ya saba duk sadda zai fita suyi musabaha. Bashi tattausan tafin hannunta tayi,wanda take kula da taushinsa sosai tun daga sanda ta gane yana daya daga cikin abinda yakeso a jikinta. Baya rabo da riqe hannunta muddin suna tare. "......For me." Ya qarasa maganan daya fada din dazu. Akhnan ta ji wani irin murmushi ya subuce mata. Sai ta kalli yaran da ke maqale da mahaifinsu. Ta kalli haisam.......tana tunanin yadda zai kasance idan ya gano abin da take zargi. Ta san abu daya kawai..... Idan ya tabbata...mutumin nan ba zai sake samun nutsuwa ba kwata-kwata sai sanda ta haifa abinda ke cikinta din. "Am....amma nace zamu samu jet?,nasan ka manta" Ta fada sanda take dab da rufe masa qofar motar. Kai ya daga yana dubanta ba tare da yayi magana ba. "Zamuje agadez....duba sultane.....baya jin dadi,aisa ma ta sakeyin miscarriage tana gida". *zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 08187255862 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 08187255862 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 159* __________________________ https://chat.whatsapp.com/BkfPzSEDhnsIwyCD8LNGkm?s=cl&p=a&mlu=0 *IDAN KINSAN BA ORDER DIN KAYA ZAKI DINGA SAKAWA BA* *IDAN KINSAN BA BUSINESS KIKE DA NIYYAN YI NA KAWO KAYA DAGA CHINA BA KARKI SHIGA* *_DON ALLAH KARKI BATAWA KANKI LOKACI_* *_Assalamu alaikum my loyal people_* *_Barkanmu da wannan lokaci,kuma barkanmu da warhaka_* *_akwai da dama cikin mata wadanda suke sha'awar yin order kaya daga CHINA zuwa NIGERIA,NIJER,CAMERON,CHAD da GHANA_* *_Amma rashin samun amintaccen company....ko hannun wanda zasu dinga siyan kaya ta hannunsu cikin aminci ya hanasu_* *_To a yau addu'ar da yawa daga cikinku ta amsu,don nayo muku tsarabar kamfanin da zakuyi siyayya ta hannunsu su kuma dora muku kayanku har qasarku cikin aminci ba tare da fargaba ko d'ar d'ar ba_* *_kunsan komai nawa TASTED AND TRUSTED ne,to wannan kamfanin idan akwai abinda yafi TASTED AND TRUSTED ma shine_* *_Baki da fargaba kota sisin kwabo,ni SAFIYYA HUGUMA na tabbatar da hakan_* *_Zaki iya kasancewa dasu group nasu,inda a nan zaki hadu da agent dinsu da CEO nasu gaba daya ta wannan link din,zaki samu bayanansu da komai da ya shafi mu'amala dasu_* *INA ME BAKU TABBACIN AMINCI DA INGANCI DA SAUQIN MU'AMALA DASU DA IZININ ALLAH,BAN TALLATA MUKU SU BA SAI DANA GWADA* *Allah ya dafa mana,yasa mana albarka a nemanmu,ya albarkaci halal dinmu ameen summa ameen* ___________________________ "I know,ina sane,ta yaya zan manta da duk wanda ke rayuwa cikin gidan nan?.....zansa su shirya jet din,ko gobe da safe sai muje. Sahel couture new branch ma yana buqatar sanya idanunki.....kamar akwai gyararraki daya kamata kiyi". " Yes sir" Ta fada tana saluting nasa. Abinda ya sanyashi sakin murmushi kenan,ta rufe masa qofar a hankali sannan taja baya,ya sauke window din kamar yadda ya saba ta tsaya sosai ta masa addu'a kamar kowacce rana idan ta rakoshi zai fita. Suka shafa addu'an tare. "Allah yayi miki albarka" Ya fada sanda ya bawa driver umarnin tayar da motar, "Ameen....." "Fi amanillah" Ya furta lafazinsa na qarshe kaman yadda ya saba fada kowanne lokaci. ★★★ *_TSAKANIN HARSHE DA HAQORI_* Gagarumin sauyi da sabbin tsare-tsare ne suka fara bayyana a tsakanin masarautar Agadez da ta Jimma qarqashin jagorancin Prince Sheikh Muhammad Haisam Aba Jifar. A cikin yan shekarun da suka biyo bayan aurensa da Khadeeja Sultane Muhammad Hammud,an samu qulla manyan alaqoqin kasuwanci, ilimi da al'adu tsakanin masarautun guda biyu. Abubuwan da a baya suke daukar watanni kafin a cimma matsaya a kansu, yanzu cikin sauqu suke samun sahalewa da cikakken goyon baya daga bangarorin biyu. Dangantakar da ta fara ne ta hanyar aure da haduwar jini, ta rikide zuwa wata gada mai qarfi da ta hada al'ummomi daban-daban, tare da qara kusantar da zukatan jama'ar qasashen biyu. An fara shirye-shiryen musayar dalibai,qwararru da yan kasuwa. Haka kuma an ƙ Qarfafa harkokin yawon bude ido da ayyukan raya al'umma, wanda ya sanya sunan Agadez da Jimma ya fara karadewa a idon duniya. Sai dai cikin dukkan sababbin abubuwan da Haisam ya aiwatar, babu wanda ya ja hankalin jama'a kamar shirin Hawan Daba na Jimma. Tun lokacin da ya halarci wasu bukukuwa a Arewacin Najeriya, ya kasance yana sha'awar yadda sarakuna ke fita cikin jama'a domin sada zumunci da talakawansu. Wannan al'ada ta burge shi qwarai. Ya yi imani cewa shugaba bai kamata ya kasance a bayan katanga koyaushe ba. Saboda haka ya gabatar da sabon tsari da zai bawa motii damar kusantar jama'arsa,musamman wadanda ke zaune a yankuna masu nisa kuma ba sa samun damar zuwa Aba Jifar Palace domin ganinsa. Daga sanda aka sanar da ranar hawan, Jimma ta sauya gaba daya. Baqi suka fara kwarara daga sassa daban-daban na Ethiopia, har ma daga qasashe makwabta. Masana tarihi suna son ganin yadda za a hada tsohuwar al'adar Habasha da salon hawan sarakunan Hausa. Masu yawon bude ido suna son zama shaidun wani sabon tarihi. Talakawa kuwa suna dokin ganin sarkinsu a cikin irin wannan biki da ba a taba yin irinsa ba a qasar baki daya. A wannan lokacin kuwa, gidan Haisam da Akhnan ya cika da baqi fiye da yadda aka saba. Babbar villar da Haisam ya gina shekara daya baya. Ya fidda sassanni daban daban masu daukan hankali da sabon salo,musamman bangaren underground villa wanda ya kasance mafi soyuwa a wurinsa. Tun bayan ya lura da irin nutsuwa da farin cikin da Akhnan take samu a can, sai ya sake sanyawa akayi ginin gidan qasan ta hanyar amfani da sabbin fasahohi da kayan alatu na zamani. Komai a gidan yana aiki ne ta hanyar fasaha. Daga ƙofofi masu gane fuska,tsarin tsaro mai amfani da basirar na'ura, har zuwa fitilu da tsarin kula da yanayin zafi da sanyi automatically kawai gidan zai sauya duka,idan dumi ko sanyi ake buqata. Ginin kuwa yana da wani irin shimfidadden tsari mai daukar ido. Kafin mutum ya ankara, kansa zai dauke shi daga abin da yake yi ya tsaya yana kallon qawatuwar wurin. Da daddare idan fitilu suka haska lambunan gidan, ruwa yana kwaranya a cikin mabubbugan da aka tsara da fasaha, yayin da iska mai sanyi daga tsaunukan Jimma ke ratsawa cikin bishiyoyi....wurin yakan yi kama da wani sashe na aljanna da aka saukar a doron qasa. Kuma a tsakiyar duk wannan ni'ima da yalwa....abin da ya fi daraja a wurin ba gine-ginen ba ne. Ba dukiya ba ce. Sai dariyar yara da ke cike da gidan,iyali daya fara tarawa me yawa,da kuma zaman lafiya da qaunar da Allah ya albarkaci iyalin haisam da Akhnan da ita. Dukka yaran falaak guda hudu....yaran shehnaz guda uku.....saina aisa guda biyu suna gidan. Haka yaran rumaisa da takanas suka taho da rumaisa sunqi zama a aba jifar palace sai nan gidan. Itama ta samu albarkar haihuwa,duka yaranta maza guda biyar,sai Anaani dake da yammata biyu qaramin namaji ne da yaci sunan ahmad sultane of agadez,yaci sunan kakansa ahmad ajani. Da taimakon sultana data fara zama 'yammata shekara goma sha biyu data hadiman gidan ta samu suka saita yaran. Kowa yaci ya qoshi,sukayi wanka suka shirya cikin kayan bacci,suka kwanta sannan ta dawo nata sashen. Ta manta rabonta data kwana a dakinta,don tuni haisam ya rabata da dukka dakunanta. Tana nan underground villa dinsa da idan ka shiga bakasan ma me yake faruwa a duniyar ba. Daga ita saishi kawai. Amma ayau din sai data ratse dakinta,ta sake wanka,ta fito fuskarta tana qyalli da sheqi da sabulun Mg's soap,wanda duk dare dashi take wanka. Wannan ya sanya fatarta ta sake gogewa da wani irin glowing da kullum sai haisam ya tanka.(0806 299 1549). Sabbin kayan bacci ta bare,wanda kusan kullum cikin sanya sabbin design take. Ba kasafai ta fita maimaice ba a dukka suturarta,ba ita kadai ba hatta da haisam dinma,har gwara yaran idan wani ya musu suna nacewa shi zasu maimaita. Idanu ta lumshe saboda qamshin turaren shuwa incense and more da yake fita a jiki,kabbasar da aka musu tun shekaran jiya ke tashi kamar yanzu aka turarasa.(+234 704 229 3387,ina sake maimaita muku,tasted and trusted ne🙌🏽🙌🏽🙌🏽). A nutse ta dauki hijab dinta kawai don sallar dare,wanda ta saba zuwa yanzu,kota tasheshi ko shi ya tasheta,ta zura lausasan slippers dinta ta soma sauka zuwa gidan qasan. Daka shiga zakasan gurin yana da banbanci da kowanne sashe na gidan. Kulawa da gyara na musamman take bashi da kanta,bata bari kowa ya shiga gurin. Har zata wuce bedroom dinsa ta fasa,ta wuce zuwa kitchen ta hada masa special tea din da yakesha duk dare don warware gajiya. Ta shirya komai da wani irin tsarin saman wani royal tray,sannan ta taka a nutse taka wucewa dakinsa. Qofar na scanning face dinta ta bude kanta da kanta cikin abinda baikai second biyar ba,ta qara turata tana shiga bakinta dauke da sallama. Yana tsaye daure da fari qal din towel me laushin gaske. Iyakarsa qugunsa,don haka wannan gymnastic body din nasa na waje a bayyane. A wannan lokacin.....ba shine ya dauki hankalinta ba. Aah....wayar dake hannunsa wanda tana sallama ya ajjiyeta saman sofa bed yana aza idanunsa a kanta. Murmushi ya sakar mata yana takowa inda take tsaye,haka kawai yau saita samu kanta da gaza jin murmushin nasa har cikin zuciyarta. Ta sakar masa tray din ta taka a nutse tana wuceshi zuwa saman sofa din. Wayar ta kalla ta dauke kai,ba abinda yake dawo mata sai kiran daya dinga shigowar wayar tasa a dazu. Ba suna a number din......amma kuma duk wanda zai kirashi wayar zata sanar masa ko waye koda bai sani ba. (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) Menelik ta gani a rubuce a jiki. Wani suna guda daya da bazai dusashe daga kanta ba. Idanunta ta dauke a hankali daga kan wayar ta maida kansa. Saita sameshi shima ita yake kalla yana sipping tea dinsa a hankali. Saqo ne ya sake shigowa,sai ya miqa mata hannu kai tsaye. Mamaki ya daskarar da ita ganin yadda yake dubanta kai tsaye. "Omar ne.....muna magana dashi network ya dauke,inda yake ba network me kyau......" Bata tsaya qarasa ji ba kawai ta bude saqon kai tsaye,kasancewar komai na wayarsa ta sani. Pin da komai....ba iya na waya ba,komai nasa dake da password ko pin ta sani. *_Muna hanyar zuwa kallon hawan Durban,koda ban samu ganinka a kusa ba....a nesa kawai ya wadatar....menelik_* ".....suna son zuwa da saamee,to amma yace batajin dadi....zai taho kawai shida yaran" Ya qarasa fada yana ajiye mug din saman table din. "Saamee?" Ta fada da sigar tambaya,kansa ya daga yana dubanta jin sound dinta ya sauya. "Ko ba saame ba?,saamee ta tafi.....amma ga wata saame dinnan" Ta fada tana wurgar da wayar gefe wani irin bacin rai yana mata tasiri. Wayar yabi da kallo yadda ta kangarar da ita,saura kadan takai qasa,kuma tabbas data fadi fashewa zatayi. "Eh saamee" Ya maimaita yana dubanta kai tsaye wani abu me kama da fushi yanason masa tasiri. "A baya saamee.....yanzu kuma menelik?,menelik dai?,wa yasan sauran dauke boye da ban gansu ba?" Ta fada wani wutar kishi tana tasiri a ranta. "Akhnan" Ya kirata a nutse yana ajiye turaren da yayi niyyar fesawa. "Ki kula da yadda kike magana" Ya fada calmly saidai ransa yana sake baci. Wata dariya ta saki wadda tafi kama da kukan bacin rai. "In kula?,wai nice ma zan kula?,Na bude saqo da idona na gani. 'Ko da ban samu ganinka a kusa ba, a nesa kawai ya wadatar...' Wannan ma ba komai bane kenan?" Ya sauke numfashi a hankali, yana qoqarin danne haushinsa. "Kin gama?" "A'a, ban gama ba." Ta miqe tsaye. "Abinda nake son sani shine, me yasa har yanzu take turo maka irin wadannan saqonnin?" "Saboda bansan da zamanta bama,don haka ban hana ta ba." Kalmar ta fito daga bakinsa cikin sauqi,da kuma dukka gaskiyarshi.....amma ta sauka a kunnenta kamar dutse. "Ban hana ta ba?" Ta maimaita cikin rashin yarda. "Eh" Ya amsa mata kansa tsaye da gaskiyar nan tasa. "To ni kuma na ga laifin saqon." Ya miƙe daga kujerarsa a hankali. "Saboda kina kallon sa da wata ma'ana daban." "To ka gaya min wace ma'ana yake da ita?" Ta jefa masa tambayar kai tsaye. Shiru ya dan ratsa tsakaninsu,ya fuskanci shaidan keson tasiri a ranta akan abinda shi baida muhimmanci ko kadan a tare dashi. Sai ya dauki wayar daga inda ta jefar, ya ajiye ta a gabanta. "Kin san password dina. Kin san komai nawa. Ban taba boye miki komai ba. Amma idan har za ki riqa neman abin da zai bata miki rai a cikin komai, ko ni kaina ba zan iya taimaka miki ba.....wannan ba komai ban....." "Mace tana cewa ko daga nesa ta ganka ya wadatar mata. Kai kuma kana zaune kana bani labarin wai ba komai bane." Ta fada da daga muryar da ya jita har tsakiyar kansa. Ya runtse idanunsa a hankali yana qoqarin controlling kansa. *_INGANTACCEN MAGANIN SANYI NE SADIDAN,WANDA BA'A CAKUDASHI DA KOMAI BA SAI ZALLAR SASSAQE DA ITATUWA MASU AMINCI_* *_KAYAN GYARA MASU INGANCI DA WARWARE MATSALAR MATA TA FUSKAR CIWON SANYI WANDA YA KASA JIN MAGANI_* *_GARZAYA A SIRRANCE KI WARWARE MATSALARKI,KI TUNTUBETA TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE_* +234 810 914 9876 *zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 08187255862 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 08187255862 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 160* _________________________ *_Amintaccen gurin siyayya_* *_ingantattun kaya akan ingantaccen farashin da ba irinsa a kasuwa_* *_BONONZA DA PROMO akai akai_* *dukka sai a HUGUMA CLOSET* *Duniyar kayan yara,mata,maza,dukka* *shaddodi,atamfofi,laces,abayas,jakankuna,takalma,agogo,sarqoqi,English wears,night wears,under wears,da duk wani nau'in sutura babba da qarami* *_Karki yadda ayi babu ke.....leqa kiga yadda closet din HUGUMA kullum ke cike da kaya akan farashi me kama da KYAUTA_* *_YAN SARI....YAN REPOSTING.....DA SARAKAN ADO MASU SIYA DON KANSU....DUKKA INA MUKU MARABA_*🤝🤝🤝🤝 https://chat.whatsapp.com/FrqgC0YmUWP4FPmUzYuLJX ___________________________ "Wannan ba maganar da ya kamata ki rikide ta zuwa wani abu daban ba ce." "To ka gaya min me ya kamata in dauka?" Ta matsa. "Ko kuwa zan jira ta zo ta tsaya a gabanka ne kafin in fahimta?" Wani irin shiru ya ratsa falon. Ya dube ta na wasu dakiku. "Ki mayar min da wayar." "Ba zan mayar ba."ta fada kai tsaye,mamaki sosai ya kamashi,abinda bata taba gwadawa ba. "Akhnan." "A'a,ba wata Akhnan,yau sai ka gaya min gaskiya." Ta ga yadda yanayin fuskarsa ya fara sauyawa, amma hakan bai sa ta ja baya ba. "Ko ita ce dalilin da yasa ka shirya Durban din?" "Ya isa." "Ko kuma kana fatan ganinta ne? Tunda ita ma ai zata zo." Ya rufe idanunsa na dan lokaci kamar mai qoqarin danne wani abu. Amma Akhnan ta ci gaba. "Ko me yasa ma ba zaka gayyace ta kai tsaye ba? Tunda dai....." "AKHNAN!" Muryarsa ta daki falon da qarfi har ta yi shiru nan take. Ya miƙe tsaye gaba daya. "Na ce ya isa!" Numfashinsa ya dan yi nauyi, idanunsa a kanta,har tsakiyar zuciyarsa yana jin quncin yadda ta tilastashi yayi abinda bai taba tunanin zaiyi ba. "Kin tambaya, na amsa. Amma ba zan zauna kina jujjuya maganata yadda kika ga dama ba......ba tsoronki nake ba....ko kadan,idan inason ganinta....ko inason gayyatarta kai tsaye....kai tsayen zan aikata hakan" Ji tayi kamar jiri zai kayar da ita,hawaye take suka cika mata idanu. Ita haisam yake gayawa haka?. Kansa tsaye?,yana kallon cikin idanunta?. Kawai saita sauke masa wayar ta doshi qofa da sassarfa tana ficewa. Komawa yayi ya zauna,yana jin wani abu mara dadi yana mamayarsa. Karon farko....karon farko kenan da wani abu mara dadi ya taba shiga tsakanin su. "Me yasa baka jure ba....me yasa baka sake kai zuciyarka nesa ba?" Zuciyarsa da ta kasa ganin laifin Akhnan ke tuhumarsa. Tunda ya kwanta bacci ya kasa zuwar masa. Fuskarta kawai yake gani cikin idanunsa da suka cika da qwalla. Amma me yasa?,me yasa zata tursasashi yayi abinda baiyu niyya ba?,abinda ba halinsa ba?. Da qyar ya taushi zuciyarsa.....ya hana kansa binta. Yanaso ta gane tayi kuskure.....yanaso ta fahimci duk girman son da yake mata idan tayi kuskure dole zai gyara mata. Da asuba yabi duka yaran mazan ya hada kansu suka wuce sallar asuba,saidai kafin su wuce din ya biya dakinta,yana kulle bata bude ba,ta cire kuma security check na qofan bare ta bude masa automatically,amma still ya mata knocking ya kuma kira sunanta. Ya tabbatar taji,don ko bacci take muddin ya kirata da sunan nan nata zata farka ta kuma amsa. Da gaske ta jishi.....don bayan ta dawo dakin tayi kuka sosai,zuciyarsa tayi sanyi sai ta soma hasaso abinda ta aikata. Itama batasan dalili ba....batasan meye yahau kanta ba.....saidai tana danganka hakan da zallar sonshi daya mata yawa....da kuma sauyin da takeji a jikinta da yake sake gaya mata anya ba ciki bane?. Kusan shigen yanayin irin na cikinsu ashraf ne,ta kasa gwadawa koda da pt stripes ne. Wani kunyarsa data rugo ta lullubeta ita ta hanata amsa masa. Kuma ko yanzu bayan ta idar da sallar asuba,a gurguje ta fita ta bada umarnin duka abinda zaayi sannan tace musu kada subar yaro ko daya ya tasheta har su wuce gurin hawan,idan ta gama abinda takeyi zata fito da kanta. Saqon da haisam yaji suna gayawa su ashraf kena da suka nufi dakin da zummar shida gaidata. Ba dashi suke ba....amma sai shima yayi amfani da wannan ya qyaleta bai sake komawa ba. Shi ya kula da komai,da taimakawar hadiman. Gidan ya cika da annuri. Tana daga daki amma tana jin hayaniyarsu. Ranta ya sake baci ganin haisam bai biyota ba,kamar ma ta manta ita ta buqaci kada wanda ya dameta. Dole ta tashi tayi wanka,ta shirya cikin wasu kaya daban ba wanda sukayi zata saka ba. Don gaba daya abun ya fice mata a rai,jin laifi da haushi kawai takeyi tattare da ita. Jin hayaniyarsu kamar kusa da dakinta yasa ta gaza ci gaba da jurewa. Da alama sun gama shiryawa. Shirin data ciwa buri,shirin data tsara ita zata shirya mijinta da kanta,sai kawai ta karya billenta,ta bude security na qofar ta fito. Sai ta tsaya cak. A falon...sanda ta qarasa fitowa. A parlour din nata.....haisam da yaransa takwas ne tsaye. Bayan yaran nasa da sauran yaran 'yan uwansa da nata 'yan uwan. Dukkansu cikin fararen shaddoji sukayi,saidai nasa da na garansa yasha banban dana sauran. Babbar riga iri daya,fara qal sai maiqo take da wani qwataccen qamshi. Dinkin anko da mahaifinsu. Kamar an zare su daga juna,kamar daga jikinsa aka dinga tsagosu,don hatta da takalmi da agogon hannunsu iri daya ne. Ashraf......asif......afeef.....ahlam.....ahsan....da ajmal. sauran 'yan matan kuma su biyu wata farar Royal abaya ce a jikinsu da yasa aka saqa musu qwaya biyu kacal saboda wannan ranar. Dukkansu suna kama da Haisam ta wata fuska. Duk da wani lokaci su yumna da ita ake cewa suna kama sak da sak. Haisam yana tsaye a tsakiyarsu,yana gyara hular Ashraf,yaron dake da wani irin tsaho kamar yanason taddo mahaifinsa ne. A jkinsa yaji fitowaeta,sai ya dago kai,idanunsu suka hadu,wani irin chemistry ya ratsa tsakaninsu me qarfin gaske. Shiru na wasu dakikoki,karon farko da suka kwana gida daya amma a mabanbantan dakuna. Ciwo ko lalura lafiya ko rashinta bata taba rabasu haka ba. "Ammeee" Yumna ta fada,t ruga gurinta da gudu,abinda ya jawo hankalin sauran suka biyo baya. (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) Nan take yaran suka kewaye ta,wani ya rungume qafarta. Wani yana gyara mayafinta. Wani yana gaya mata ya fi kowa kyau yau,duk sai taji kewarsu ta cikata. Haisam kuwa yana kallonta ne kawai. Da wannan murmushin nasa. Yana jin wani tausayinta yana ratsashi. A jiyan baiyi baccin kirki ba. Ya kwana ne kawai yana tuhumar kansa,inda daga qarshe ya kwana yana sallah kawai. Sanda ya tuna wani zargi daya darsu a ransa tun rannan,sai yaji kaman ya tashi cikin daren ya bita,amma bayason tayar da ita. "Anya ba ciki bane?" Tambayar data sanyashi yayita nanatata daga qarshe ya aminta da hakan. Saboda ya sani....wannan akhnan din wata akhnan ce daban,ba a banza tayi masa haka ba,yayi imani da wannan ya sani sosai. Shine na farko da zai shaidi matarsa. Bashi kawai ba....koda takalminsa da yake sanyawa girmamashi take ballantana shi. Ruqayya ce ta shigo ta tattara kansu suka fice,a mota zasu isa jimma palace kafin a nadawa kowa rawaninsa,a bashi dokinsa,dawakan sa already suna dasu kusan uku uku kowa ke dashi. Bayan yara sun fita zuwa motocinsu...sai ya rage su biyu. Tare suka miqe zuwa ga juna,amma sai ya tsaya ganin ta nufoshi. A hankali Haisam ya soma takowa shima,yayi saurin kamota sanda ta zame zata zube gwiwarta a qasa. Dagata yayi zuwa jikinsa yana qoqarin lalubo qwayar idanunta amma kunyarsa tasa ta kasa bashi dama. So take ya qyaleya ta tsugunna gabansa ta bashi haquri. "Har yanzu kina fushi?" Akhnan ta gyara mayafinta a kunyace. "Ban ce haka ba." Ta fada a shagwabe tana cikin jikinsa,wannan lallausan qamshin nasa yana shige mata hanci. "Akhnan." Ta qi kallonsa. Sai ya dan sunkuyo kadan yana murmushi me sauti. "Habibti."Har yanzu ta qi kallonsa. Kunya takeji......amma da alama baima gane ba. Sai ya yi dariya qasa-qasa. "She called."Shiru. "I didn't."Har yanzu babu amsa. Sai ya matso da ita yana manneta da jikinsa,qamshin shaddarsa.....da qamshin turarensa suna bada wani kalar qamshi me taushi. "After all these years..."Muryarsa ta yi qasa. "...you still don't know who owns my heart?" A wannan karon ta kasa hana kanta kallonsa,ta ware blue eyes dinta sosai a kansa. Sai ya nuna yaran da suka riga suka fita. "Eight children." Sannan ya nuna kanta. "And still jealous." Murmushi ya subuce mata duk da qoqarinta na hana kanta tayi murmushin. Nan take ya gane ya yi nasara,tasa hannu ta daki qirjinsa a tausashe. "Kayi haquri please" Bakinta ya toshe da nasa kadan,yadan tsotsi lips dinta sannan ya janye. "Karki wani nema afuwa.....menelik ce.....tun daren jiya na miki maganinta." Idanu ta waro waje. "Yes.....ya zan zauna ta jawomin jagwal. Ashe ba haisam dinki tazo turawa ba.....itama ta samu nata haisam din. Tayi saving same name ni dashi,zai kuma zo Durban din,ta ban haquri,tace zata hadamu don na tabbatar,ta kumayi deleting number mijinki,shikenan?" Ya fada yana jan hancinta kadan. Sosai ta sakejin kunya,tayi qasa da kanta tana boyewa,ya saki murmushi me laushi "......the game is over.....chapter closed..... Khadeeja ta mallake Muhammad haisam....." *zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 08187255862 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 08187255862 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽 💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 161* _________________________ https://chat.whatsapp.com/BkfPzSEDhnsIwyCD8LNGkm?s=cl&p=a&mlu=0 *IDAN KINSAN BA ORDER DIN KAYA ZAKI DINGA SAKAWA BA* *IDAN KINSAN BA BUSINESS KIKE DA NIYYAN YI NA KAWO KAYA DAGA CHINA BA KARKI SHIGA* *_DON ALLAH KARKI BATAWA KANKI LOKACI_* *_Assalamu alaikum my loyal people_* *_Barkanmu da wannan lokaci,kuma barkanmu da warhaka_* *_akwai da dama cikin mata wadanda suke sha'awar yin order kaya daga CHINA zuwa NIGERIA,NIJER,CAMERON,CHAD da GHANA_* *_Amma rashin samun amintaccen company....ko hannun wanda zasu dinga siyan kaya ta hannunsu cikin aminci ya hanasu_* *_To a yau addu'ar da yawa daga cikinku ta amsu,don nayo muku tsarabar kamfanin da zakuyi siyayya ta hannunsu su kuma dora muku kayanku har qasarku cikin aminci ba tare da fargaba ko d'ar d'ar ba_* *_kunsan komai nawa TASTED AND TRUSTED ne,to wannan kamfanin idan akwai abinda yafi TASTED AND TRUSTED ma shine_* *_Baki da fargaba kota sisin kwabo,ni SAFIYYA HUGUMA na tabbatar da hakan_* *_Zaki iya kasancewa dasu group nasu,inda a nan zaki hadu da agent dinsu da CEO nasu gaba daya ta wannan link din,zaki samu bayanansu da komai da ya shafi mu'amala dasu_* *INA ME BAKU TABBACIN AMINCI DA INGANCI DA SAUQIN MU'AMALA DASU DA IZININ ALLAH,BAN TALLATA MUKU SU BA SAI DANA GWADA* *Allah ya dafa mana,yasa mana albarka a nemanmu,ya albarkaci halal dinmu ameen summa ameen* __________________________ ".....abbee" "Don't.....karki musa" Ya fada yana daga hannuwansa sama duka biyun. "....coz ni na yarda....saboda...." Sai yadan tsaya. "......dama a mallake nazo wallahi" Dariya suka saki shi da ita,sai ya jata jikinsa a karo na biyu yana manna mata tattausan kiss. "Khadeeja zaki haifo in sha Allah....da alama kuma rigimarki zatayi,so stay at home,banaso kiyi stressing kanki,zan saka a saka miki device,zakiga komai kamar kina gurin....after an gama,zan tattaro duk wanda kikeson gani na kawo miki shi nan......ko waye....." Kai kawai take girgizawa. Yana fasa mata kai da yawa. Tana jin kamar gatan ya mata yawa. "Abbee" Ta kirashi sanda yakai bakin qofa tana qare masa kallo. Ya waiwayo yana dubanta da manyan fararen idanunsa. "Kayi kyau......" Murmushi ya subuce masa. "Kuma haka zasu gani su haqura su barwa khadeeja ni ba" Dariya sosai ya sanyata harda hawaye. "Ka yafemin" Ta sake fada. "Don Allah....bazan sake ba" Juyowa yayi gaba daya yana dubanta. "Da laifin da kika taba yi duk da baki dashi ma.....da wanda kikayi yanzu....dama wanda zakiyi a gaba.....muddin bai sabawa fadar Allah ba,indai haqqina ne na yafe to na yafeshi....." Maganansa ta qarshe kenan ya juya yana fita ya barta da zuciya me nauyi,zuciya me cike da soyayya. ★★ Daukacin ilahirin unguwar bama masallacin kawai ba......ba abinda kakeji daga manyan sifikun da masallacin mafi kyau girma da daukan hankali ke fita sai lallausan sautin karatun qur'ani da muryar fitaccen malamin addinin nan.....kuma jinin sarauta yarima muhammad haisam aba jifar. Daren ashirin da bakwai ne ga watan ramadan. Daren da duka musulmi suke bawa muhimmanci tare da qarfafa zaton samun daren lailatul qadr a cikinsa. Duk da ba wani nassi kai tsaye daya bada tabbacin cewa eh shine daren. MASJID ASSAKEENA.....masallacin da kaf unguwar da kewayenta ba masallaci irinsa. Wani irin gini aka masa me daukan hankali qwarai,taswirar masallacin haram na madeena aka dauko aka tsara masa gini me kamanceceniya dashi. Ya dace da gurin dama unguwar ta masu hannu da shuni qwarai,saidai duk da yawan security da unguwar ke dashi saboda wanzuwar yarima haisam din a cikinta,hakan bai hana mutane daga nesa zuwa masallacin yin sallolin farilla guda biyar ba. Har ma da sallah juma'a ake gudanarwa. A yanzun da aka cikin watan azumin ramadan kuwa. Wani irin cika masallacin yake ba masaka tsinke,masallacin dake da sassa biyu manya manya. Sashen maza dama sashen mata,wanda shima aka qawatashi sosai kamar sauran sasannin na masallacin. Ba kyan masallacin kawai ba. Abu mafi jan hankali a masallacin bayan tsaro da yake dashi,kyau da tsari na shayar da masallata ruwa me kyau da lemuka harma da shayi......limaman masallacin. Qananun matasan 'yan ukun masu abun burgewa. Jinin masarautar jimma....jinin masarautar gumma. 'Ya'ya ga yariman matashin nan sheikh muhammad haisam,wato muhammad muhammad haisam(ashraf). Da ibraheem muhammad haisam(aseef). Da kuma mahmud muhammad haisam (afeef). Dukkaninsu shekarunsu na haihuwa tsakanin goma zuwa sha daya. Amma kowannensu mahadacci ne na alqur'ani me girma. Ba iya haddar kawai ba,qira'o'i ne kala kala suka iya,ba wadda basa yi cikin qira'o'in nan guda bakwai sanannu. Hakanan kowannensu akwai launin sautinsa,yadda yake sarrafa qur'ani a harshensa da yasha banban dana dan uwansa. Asharaf yana yin qira'ar sheikh badr al turki,kuma da yake yana da miskilanci sai qira'ar ta dace da yanayinsa sosai. Asif ne yake qira'ar sheikh yasser aldosari. Yana qaunar malamin tun asali,wannan ya sanya ma haisam sai daya tafi dashi umra suka gaisa. Afeef qira'ar sheikh sa'ud shuraim yakeyi,wadda kusan dukka cikinsu best qira'ar ammensu akhnan kenan idan ka cire asali ta mahaifinsu. Wani dadi nutsuwa da kwanciyar hankali takeji a duk sanda take sauraron karatun yaran nata. Kaman yanzun......bayan da haisam ya idar da raka'o'i biyun farko kaman yadda suka saba. Yakan fara budewa ne da nasa jagorancin,sai ya matsa baya ya bawa daya daga cikinsu. A yau din afeef ya kalla,don ya fisu sauri sauri a karatu. Duba da yadda masallacin yake a cike da mutane,akwai buqatar sassauta tsahon tsaiwar sallar kamar yadda addini yakeso. Suna jere ne a bayansa,dukkaninsu sanye da farar silk jubah da mayafin nan da larabawa ke dorawa saman kansu,wadda hasken fararen qwayayen da suke tarwai a masallacin suka fidda kyanta da sheqinta da tsadar da take dashi. Kai yaron ya rusunar alamun girmamawa ga mahaifinsa,sannan ya taka a hankali yahau saman abun sallar inda haisam din ya sauka. "Allahu akhbar" Muryarsa me cakude da yarinta kadan ta ratsa ta mic din ta raba wani irin nutsatsten sauti zuwa kowanne sashe na masallacin dama uguwar gaba daya. "Alhamdulillahi rabbil Aalameeeeennn". Ya soma da suratul fatiha. Sautin daya ratsa da wata irin nutsuwa ya kaiwa akhnan dake tsaye itama cikin tarin kushu'i saman abun sallar ta. Cikin private musallah dake wani bangare dake manne da masallacin a cikin gidansu. Ita da sauran hadimanta ne duka da ma'aikatanta mata,wadanda suka kusa su ashirin. Aikinta ne wannan,bata sake dashi. Duk wanda ke qarqashinta sai ya tashi wannan ibadar indai ba uzurin al'ada irin na diya mace ba. Cikin taimakon Allah.....sai itama Allah ya hadata da masu son ibadar,ance kamanninka kamannin mutanen da kake rayuwa dasu,kuma zama da madaukin kanwa shike kawo farin kai. Sun riga sun tasirantu da kyawawan dabi'u irin na iyayen gijin nasu sheikh haisam da akhnan. (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) Idanu ta lumshe a hankali,tana jin wani alfahari da yaran nata. Tana jin wani tarin godiya ga ubangiji bisa ni'imar da yayi mata. A duk sanda zata wuce ta dakinsu,kota garden na gidan taji suna musaffa sai taji hawaye ya cika idanunta. Ko iya irin wadannan yaran da haisam yasa ta haifa.....ta kawowa duniya kyakkyawan iri....kyakkyawan misali....me zai hana ba zata kirashi da suna ALMAZ BA?(lu'u lu'u). Wani lokaci takan jima tana kiranshi da LU'U LU'U din,idan kuma ya juyo ya kalleta sai ya sake mata murmushi. "Ke kika cancanci wannan sunan da kika bani rassa masu kyau.....dukkan bishiya me kyau ita ke fidda 'ya'yan itace masu kyau". A yanzun hatta dasu ahsan sun dauki hanya,sunyi nisa a tasu haddar,a sanda kuma su asif kowanne haisam ya fidda tsarin makomarsu da yake tunanin zasu zama a gaba. "Kita musu addu'a,Allah ya hukunta musu alkhairi a abinda na zaba musu,addu'ar uwa nada kaifi sosai" Takanyi murmushi,abun ita kanta da take uwarsu yana burgeta sosai. Sun samu fasihin uba,wanda gobensu da jibinsu yake kallo,ba jiya da yau ba. Yakan ce "Shi ashraf,shine babba,first born....ina masa sha'awar business Administration + Economics,shi ne babban magaji. Shi yasa nake tafiya dashi meetings. Yana kalla,yana koyon shugabanci,kuma yana fahimtar yadda ake tafiyar da kamfanoni. A nan gaba shi ne zai zama shugaban empire dina gaba daya. CEO na haisam group of company in sha Allah" Murmushi tayi a sannan tana jinjina kai. "In sha Allah" Itama ta mainaita. "Sai Afeef (Mahmud),The Innovator Computer Science + Artificial Intelligence. Afeef yana da basira sosai da naci akan duk abinda yakeso ya koya....nasan kema kin lura,inaso nan gaba ya zama me gina software. Yana son cybersecurity tun yanzu na lura,sannan yana son robotics. Kin gane hikimar zamanshi a haka?" Kai ta girgiza. "Good.....Shi ne zai mayar da empire din ta zamani,kowanne zamani aka shiga zai sanyata ta dinga tafiya daidai dashi" Kai ta jinjina. "Idan Ashraf ya gaji empire din, Afeef ne zai kai shi gaba." Murmushi ya sake balle mata,saboda yadda taji hikima a tsarinsa sosai. "Sai Asif(Ibraheem),The Diplomat International Relations + Law,ya iya magana baba na sosai......ya iya sasanta qannensa tun yanzun" Dariya tayi sosai. "Son kai ko?" Girarsa da kafadarsa gaba daya ya dage yana karyar da kai. "Gaskiya ce....ke mamarsu ai kin fini sanin hakan" Kai ta gyada tana murmushi "Haka yake" "Bana fatan suyi siyasa.....amma idan Allah ya qaddara masa shigarta.....zan tabbatar ya zamana na daban a cikin su me kawo gyara,bame neman wani matsayi ko muqami ba. Dole a akwai hulda da sarakuna da shugabanni. Akwa wakilci duk zai iya shiga ciki,kinga zai taimaka sosai wajen tafiyar da ragamar gidan nan dana masarautar kakansa.....idan kuma likitanci ya zaba....nafi masa sha'awar cardiology ko surgery saboda ceton rayuka" "Allah yayi musu zabi mafi alkhairi" Akhnan ta fadi zuciyarta na mata sanyi gami da qara alfahari da iyalin nata. Sai kusan hudu aka kammala sallar,ta sanya ruqayya ta sauke mata su yumna da sukaqi yarda su kwanta a dakinsu. Yawanci idan zata fito sallar da ruqayya suke zama a dakinsu,amma idan fa suka farka to sai gurinta kuma. *zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 08187255862 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 08187255862 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *BOOK 03///PAGE 162* __________________________ *_Amintaccen gurin siyayya_* *_ingantattun kaya akan ingantaccen farashin da ba irinsa a kasuwa_* *_BONONZA DA PROMO akai akai_* *dukka sai a HUGUMA CLOSET* *Duniyar kayan yara,mata,maza,dukka* *shaddodi,atamfofi,laces,abayas,jakankuna,takalma,agogo,sarqoqi,English wears,night wears,under wears,da duk wani nau'in sutura babba da qarami* *_Karki yadda ayi babu ke.....leqa kiga yadda closet din HUGUMA kullum ke cike da kaya akan farashi me kama da KYAUTA_* *_YAN SARI....YAN REPOSTING.....DA SARAKAN ADO MASU SIYA DON KANSU....DUKKA INA MUKU MARABA_*🤝🤝🤝🤝 https://chat.whatsapp.com/FrqgC0YmUWP4FPmUzYuLJX ___________________________ Ta sani,bazai shigo gidan ba sai bayan sallar asuba. Yawanci a can sukeyin sahur da abincin da yasa ake dafawa kuma a raba duk me sha'awa ya zauna yayi sahur a masallacin. Lafiyayyen abinci ne kamar a gidanka,don ko a gidanka abinda zakaci kenan,da shayi dai da ruwa da drink,saboda wasu nada dan nisa,kafin su isa gida suyi sahur lokaci ya qure musu. Wannan tsarin masallacin daban yake,kusan ya ciri tuta kuma yayi suna. Hakanan tasirin albarka da addu'ar da haisam din ke samu ne na jama'a keta bibiyarsa shida iyalinsa. Yakan gaya mata cewa. "Ko bayan na mutu.... Ki riqe ciyarwa,ba abinda Allah keso sama da ciyarwa. Ciyarwa tana bude qofofin arziqi da alkhairi ga dan adam me tarin yawa,tana rufe qofofin tsiya dana azaba sosai" Murmushi take ta gyada kai,ta yarda da wannan tuntuni. Ciyarwar da takeyi duk juma'a tun tana akhnan dinta,me izza da jin sarautarsu tafi ta kowa......a kullum tana kyautata zaton qilan ita kadai Allah ya duba cikin ayyukanta ya karba ya mata kyautar haisam din. Banda haka batajin tana da wani aiki da zata samu wannan ladan. Bayan sun gama sahur a Masjid As-Sakina, suka fito cikin sanyin iskar qarshen dare. Yaran suna zagaye da Haisam suna masa hira. Ashraf ne ya ja sallar Fajr a wannan asubahin. Muryarsa ta cika masallacin da wata nutsuwa mai kama da ta mahaifinsa shekarun da suka gabata. Da suka shigo cikin gidan,akhnan tana jiransu. Don bayan sahur bata kwanciya har sai taga shigowar haisam. Fuskarta cike take da farin ciki da annuri wancan irin farin cikin da bai taba gushewa ba muddin zata ji sautin muryoyinsu suna karanta Al-Qur'ani a masallaci. Tun daga nesa ta hangosu,haisam a gaba,yaransa shida a bayansa banda su yumna dake daki suna bacci. Kamar wata qaramar rundunar sarakuna haka idanunta ke gane mata tattare dasu. Sai ta jingina da bakin qofar parlour tana kallonsu. Ba tare da ta ce komai ba......haisam ne ya fara lura da ita. Murmushi ya bayyana a gefen bakinsa. "Why are you standing there?" Ya fada da muryar nan da ko yaushe take taushi idan zai magana da ita. Kusan narkewa take idan taji muryar,akwai randa ta riqeshi gam suna cikin yara,Allah yasa sun juya suna ficewa. "Haisammm manaaa" Ta fada a shagwabe,shi da ita duka idan suna abu kaman basu ajiye yara haka ba. "Akhnaaaannn.....me kuma?" "Kana sani ina narkewa......don Allah abbeee....wannan muryann....hmmmmnnnn". Murmushi ya saki,ya kamata a nutse ya zaunar da ita,sannan ya zauna kusa da ita. " Bazan iya daga miki murya ba my princess....bazan iya ba,kada ma Allah ya kawo ranan....manzon Allah ne yace rifqaan bilqawarir,ma'ana kuyi hankali da abun qarau dinnan,kaman abu na glass....kinsan me yake nufi?" Saita girgiza kai tana murmushi. Ta karanta ta sani ta gani,amma a bakinsa kawai takeso taji. Kota karanta nassi ko tarihi,tafiso taji ta a bakinsa,yana wani irin shigarta ne da zauna mata a kai. "Manzo S A W ya kwatanta zuciyar diya mace da tangaran ko glass saboda rauninku,yaya zan iya miki magana da irin muryar da nake magana da kowa?....kamar ke din bata musamman bace?" Wani lallausan murmushi ne ya subuce mata,ta boye fuskarta saman kafadarsa tana dariya. "Kai kam ko....Allah ya maka baiwar iya koyarwa....kai din malami ne na haqiqa". "Karatu kawai na iya na takarda....ko harda wancan daya karatun?" Ya tambayeta muryarsa can qasa da wani yanayi daya sanya duka tsigar jikinta zubawa. Ruqunqumeshi tayi tana qyalqyala dariya,don da iya maganar kawai ya tsumata gaba daya. Dama haka yakeso.....irin cikin su ashraf ne.....kai tsaye ya dauketa suka wuce can matattarar sirrinsu. Kama yatsunta da yayi ya dawo da ita daga tunanin,sai ta girgiza kai a hankali. "Nothing." Ta amsa tambayarsa,amma murmushinta ya qara fadada. Ashraf ne ya karaso kusa da ita. "Ammiee." "Hmm?" "How was it?" Ta san abinda yake nufi,kowace rana idan ya ja sallah. Sai ya tambayeta. Sai ta kamo fuskarsa da hannunta,kamar yadda take yi tun yana qarami. "It was beautiful ashraf......barakallahu feek" Idanunsa suka yi haske da wani farincikin yabo daga mamar tasa. Uwar da sukewa wata irin tarin qauna tun suna qananunsu har zuwa yanzu da suka qara hankali. "Every time I hear your voice..." Sai ta dan yi shiru "...I remember the little boy who used to sleep on my chest." Su asif suka fara dariya. "Not again." Ahsan ya fada. "Mama always says that."ajmal yace shima. "Because it's true." Ashraf ya fada yana gyada kai cike da qaunar ammiee din tasa Tsaiwa kawai haisam yayi yana kallonsu,idanunsa cike da wani irin natsuwa. Akhnan ta waigo ta hada ido da shi,na dan lokaci babu wanda ya yi magana. Sboda babu buqatar magana,magana ce yawancin lokuta sukeyi tsakanin zukatansu. Shekaru da yawa sun shude. Sun sha gwagwarmaya. Sun sha hawaye. Sun sha farin ciki. Amma a wannan lokacin...da yaransu suna kewaye da su. Da sautin Al-Qur'ani har yanzu yana yawo a kunnuwansu. Da Ramadan ya sake hada su a teburin sahur. Akhnan ta ji kamar Allah Ya amsa addu'ar abinda ta fi so a rayuwa. Sai ta matsa kusa da Haisam.....ta sauke kanta a kafadarsa. "Alhamdulillah." Sai ya sumbaci goshinta a hankali. "Alhamdulillah." Kuma a karon nan... ba ta fadeta ne saboda dukiya. Ko sarauta. Ko nasara. Ta fada ne saboda tana kallon mijinta da yaranta.....ta san cewa wannan shi ne mafi kyawun arzikin da Allah ya taba ba ta. *Alhamdulillah!*🎉🤍 🌹*SAƘON GODIYA*🌹 *_Assalamu Alaikum wa Rahmatullah_* *Da farko* *_Alhamdulillah da yardar Allah da taimakonsa muka kawo qarshen Lu'u Lu'u._* *_Kalaman godiya ba za su isa su bayyana irin farin cikina da jin daɗin da nake yi ba saboda qauna_* *_addu'o'i, sharhi, gyara, da goyon bayan da kuka nuna min tun daga farkon wannan tafiya har zuwa yau._* *_Ga duk wanda ya karanta, ya yi comment,ya yi addu'a, ko ya kasance cikin masu jiran sabon page da doki, ina muku godiya daga zurfin zuciyata. Kun kasance wani babban bangare na nasarar wannan littafi._* *_A wasu lokutan nakan gaji, nakan rasa qwarin gwiwa, amma kalamanku masu dadi da qarfafawa sukan sa ni ci gaba da rubutu. Wannan littafi ba nawa kadai ba ne, na ku ne tare da ni._* *_Ina roqon Allah Ya saka muku da alkhairi, Ya sanya abin da kuka karanta ya zama sanadin farin ciki da albarka a gare ku, Ya kuma hada mu a cikin alkhairi a ayyuka masu zuwa._* *_Ku yafe min duk wani kuskure da kuka gani a cikin rubutun, domin kamala ta Allah ce kadai._* *_Da fatan za ku ci gaba da kasancewa tare da ni a dukkan tafitar rubuce rubuce na na gaba._* *_Na gode. Na yaba. Ina Qaunar ku saboda Allah._* 🤍🌹 *FI AMANILLAH*🙌🏽🙌🏽 ✍️ *Safiyya HUGUMA* 08187255862