[01-16, 11:53 DARMA😍🍬 *_Typing📲_* *_💦KIƊA A RUWA...!!💦_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_GENERAL FICTION_* _Wannan labari ƙirƙirarre ne. Sunaye, wurare, da abubuwan da suka faru duk ƙirƙira ne, ba su da alaƙa da gaskiya ko wani, koda Bilyn Abdull ce 😂._ *_BOOK 2_* _Chapter 1_ __________________ Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/D1ZOZr50SfwCQUbhMB0eVC CEO Maryam Tofa 07010346400 inshaAllah zakiyi dariya kayanmu nada sauki da inganci kedai kiyi joining group din don ganewa idonki kaya masu kyau da aminci. Akwai GHT Supplements masu inganci.Allah yasa damu da alkhairi. __________________ *_TELEGRAM GROUP_* https://t.me/+erpSeN2ssqgwYTdk *_WHATSAPP CHANNEL_* https://whatsapp.com/channel/0029VbBMI7RLY6d9zU893c1F *_TIKTOK_* https://vt.tiktok.com/ZSDkPqMm1/ *_INSTAGRAM_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv ______________________ .........*_Yau da gobe ita ke canja WANE zuwa WANE bisa yarda da HUKUNCIN UBANGIJI. Ƙaddara ƘAWA ce, kamar yanda JARABAWA ke zama aminiyar numfashi da gangar JIKIN ƊAN ADAM. Idan JIYA tazo da nasara, ba lallai GOBE tazo da nasarar ba. Sai dai hakan baya nufin baza'a sake yin NASARAR ba. Kalubale shike zama tubalin da ke gina mutum har ya zama mai ƙarfi a bayan ƘADDARIRINSA. Sai dai hakan baya tabbata sai idan ka koyi haƙuri. Duk wanda ya koyi haƙuri tabbas zai mallaki rabin nasarar rayuwa. Dan hakuri shi ne ginshiƙin da ke taimakon duk wani buri ya zama gaskiya..._* Zaku fahimci abinda nake nufi ne kawai idan kuka kasance da littafin *KIƊA A RUWA__MAI* *TADA HANKALIN DODO* _kashi na biyu. Da zai fara zuwa muku_ *_Akwai Audio da zamu fara ɗorawa shima in sha ALLAHU saboda masu ciwon ido da basa iya karatu dama marasa juriyar bibiyar dogayen labaran mu. Shima Audio ɗin zai zo a AREWAPEN, da TELEGRAM akan farashi mai rahusa._* <<<<<<%>>>>>> ★2016★         Shekaru uku da wasu watanni kenan da kama Zak-Shadow. Abubuwa da yawa sun faru marasa daɗi harma da masu daɗin ta wani fannin. Sai dai rinjayen marasa daɗin ya danne masu daɗin ta yanda har idanu basa ganinsu. Misalta kalar tashin hankalin da su Mammah suka shiga a wancan lokacin ɓata baki ne. Babu irin shigi da ficin da Imran baiyi ba amma ko damar ganin Zak-Shadow an hana musu har na tsawon watanni. Daga baya shima Imran ɗin suka kama shi.       A farko manyan sojoji da yawa sun tsaya akan case ɗin da son ganin abubuwa sun dai-daita Zak-Shadow da Imran sun fito, sai dai daga baya sai suka fara janye jikinsu baya aka bar General Yusuf kawai da gwagwarmaya. Dan har cikin ransa ƙauna ɗaya tak yake ma Zak-Shadow da Imran. Faɗi tashin COAS yasa aka fara shirin miƙa case ɗin kotu, a lokacin Zak-Shadow nada watanni tara a rufe, kuma har lokacin ba'a taɓa barin kowa ya gansa ba sai masu tsaronsa sai shi COAS ɗin kawai.        Kasancewar al'amarin shiri ne na musamman da kowa ya rasa bakin zarensa a zaman farko na kotun aka yanke hukunci. Sun yanke ma Haysam Abdul-rasheed Shehu Kobi hukunci zaman gidan yari na shekara ashirin da biyar, shi kuma Imran Abbas shekara biyar. Ya rabbi wannan al'amari ba zuri'ar Mammah da gidan su Imran kawai ya girgiza ba, ƙasa gaba ɗaya ce ta girgiza, dan a take matasa masu kishin ƙasa da wasu kungiyoyi suka fara zanga-zangar lumana akan basu amince da hukuncin da aka yankema Zak-Shadow da Imran ba. Wannan zanga-zanga taso kawo hargitsi daga baya, hargitsin kuma ba kowa ne ya haddasa shi ba sai ƙungiyar duhu da suka fuskanci ana neman warware musu nasararsu. An saka matakan tsaro masu tsauri daya tilasta matasan komawa gida aka koma ka-ce-na-ce a media kawai, tare da addu'ar neman ɗauki ga UBANGIJI, Sai gargaɗi ga ƴan siyasa akan ALLAH ya kaimu zaɓe na gaba, dan duk mai hankali ya kalli abinda ya farun da idon basira yasan lallai hukuncin nan na siyasa ne kawai...       A ɓangaren Mammah ba'a magana. A wannan karon duk dauriyarta da iya danne abu sai da ta kwanta jiyya, kusan watanta biyu kafin ALLAH ya bata lafiya, sai dai ciwon hawan jini ya riga yayi tasiri a gareta. Hakama ƙannensa da sukafi kowa ɗaga hankalinsu, sai da takai har su Ma'aruff suka ce sun fasa aurensu da ake gaf da yi, amma Mammah tace bata yarda ba bata amince ba. Dan haka tana samun lafiya aka hau shirye-shiryen bikinsu, dama gininsu tun kafin a kama Imran ya dawo da shi anan cikin gidan, bayan an kama shi kuma Uncle Nasiru ya tsaya akai aka cigaba bisa shawarar Mammah. Satin Mammah ɗaya da baro asibiti, da yay daidai da sati biyu ciff da yankema su Dada hukunci akai bikin Ma'aruff da Ja'afar, sai dai bikin baiyi wani armashi ba, dan aure kawai aka ɗaura amare suka tare. Idan ka cire yara irinsu Nimrah dake shagalinsu kowa ƙarfin hali kawai yake, har dai akai aka tashi lafiya...      Kasancewar ba wani taro akai sosai ba gidan shiru babu hayaniya, su Gwaggo Khadijah ne dama kawai sai wasu tsiraru daga mutanen Kano suka zo. Tun bayan sallar isha'i aka maida amare sashensu, dan tunda aka kawosu anan sashen Mammah aka ajiye su sai yau da biki ya tashi. Ganin har ƙarfe goma babu Ma'aruff babu Ja'afar Mammah tai kiran Bilal tana tambayarsa su.         Amsa ya bata da, “Mammah gasu nan fa a ɗakinsu. Da alama kuma basu da niyyar tafiya sashensu. Wanka ma da ƙyar na samu sukayi suka canja kaya”.          Murmurshi Mammah tayi tana ɗan girgiza kai cikin danne damuwa, “Kaga basu wayar”.     Da to ya amsa mata, yana nufar ɗakin su Yaya Ma'aruff ɗin dake jikin nasu shi da Ammar. Sai da yay knocking ƙofar suka bashi izinin shiga sannan ya shiga da sallama. Mammah dake saurarensa tace, “Saka wayar a amsa kuwwa”.       Sakawar yay kamar yanda ta bashi umarni, ya sanar mata ya saka. Kai tsaye ta furta, “Ma'aruff! Ja'afar!”.       A tare suka amsa mata, dan suna zaune ne a bakin gado su duka, “Yanzu kuna ganin abinda kuke shirin yi dai-dai ne kenan?. Karku manta yanzu suna da hakki a kanku, ɗaya kuka tauye sai ALLAH ya tambaye ku. Abinda kukeyi bashi zai dawo da Imran da Muhammad cikinmu ba, miyasa bazamu karɓi ƙaddara muyi haƙuri bane. Addu'a itace maganin komai. Dan haka ina baku umarnin tashi ku wuce Bilal da Ammar su raka ku sai da safe...”         Ma'aruff da idonsa ya kaɗe murya a cinkushe ya ce, “Amma Mammah.....”      “Bana son jin komai, ku tashi ku wuce kawai. Bilal kaje kai da Ammar ku rakasu.”      “To Mammah”. Bilal ya amsa yana share hawayen da suka cika masa ido. Dan Ja'afar ma kuka yake. Haka shima Ma'aruff ɗin gefe ya kauda kansa ya share nashi. Babu abinda ke cizon zukatansu sai tuna yanda suka shirya wannan ranar da ɗokin zuwanta tare da Dadansu da Yaya Imran, amma sai gashi yau anyi komai babu su, kuma suna raye, suna a gari ɗaya amma ƙaddara tai musu shamaki. Ba yanda suka iya dole sukabi umarnin Mammah, dama sunyi wanka, suka shirya cikin kayan barci iri ɗaya dan basa wani buƙatar wasu kaya saɓanin waɗan nan.      Ammar da gaba ɗaya baida isashiyar lafiya tunda aka yanke hukuncin nan nasu Dada da ƙyar ya iya binsu saboda umarnin Mammah. Ma'aruff shine babba, shi suka fara takawa har falon sashensa daya ƙawatu da kayan more rayuwa, babu abinda ke tashi sai ƙamshin sabbin kaya dana turare da sabon fenti. A ƙofar bedroom ɗin da yake da tabbacin Lailah na ciki yay knocking, bai jira amsarta ba ya buɗe kaɗan ya leƙa. Hangota can a kan katafaren gadon da aka saka mata ya sashi ɗan sauke numfashi, kafin ya buɗe ƙofar gaba ɗaya yana sallama. Bai damu data amsa ba, ya juyo yana kallon su Ja'afar da ke tsaye.     Nuni yay musu su shigo, dan haka suma duk sukai sallama ya amsa sannan suka shiga. A bakin gadon ya zauna kusa da ita, su kuma suka zauna a sofa ɗin ɗakin su duka. Duk da sun girmeta, matsayin ƙanwa take ma a garesu, dan uwa ɗaya uba ɗaya take da Imran, itace autarsu ma. Amma a tare matsayin matar Yayansu a yau suka fara gaisheta.      Da sauri ta girgiza kanta tana share hawaye batare data buɗe fuskarta ba. Dan itama dai irin ciwon dake zuciyarsu shine a tata zuciyar. Cikin rawar murya ta gaishesu batare da ta amsa gaisuwar da su sukai mata ba. Dan kai tsaye ta ce, “Yaya ina yininku”.     Amsa mata sukai da kulawa, kafin Ja'afar yay mata gajeruwar nasiha da addu'a. Shima Bilal yay mata a taƙaice. Ammar dai kasa cewa komai yayi sai addu'a da fatan zaman lafiya. Cikin abinda bai fi mintuna goma ba suka kammala suka fito zuwa sashen Ja'afar...    A sashen Ja'afar ɗin ma dai shine yay musu jagora har bedroom ɗin Shariffat. Itama dai komai na funichars ɗinta irin na Lailah ne, kala ce kowa wadda yake so aka saka masa. Ga ƙanshin turare na tashi kamar dai sashen Lailah ɗin. Ita kam a kwance suka sameta, sai da Ja'afar ɗin yay sallama sannan ta tashi zaune, fuskarta na lulluɓe itama cikin lifaya. Suna zama ta fara gaishesu. Suka amsa mata da kulawa. Yanzu kam Bilal ne yay mata nasiha ita, Ammar yay addu'a. Anan ma basu wuce mintun goman ba sukai musu sallama suka fito...        Kamar haɗin baki su Ja'afar na fita a sashen Ma'aruff Lailah ta saki kukan da take riƙewa. Haka ma su Bilal na fita Shariffat ta fashe da kuka. Dan su dukansu auren nan tamkar fami ya zama ga damuwar family's ɗin nan nasu guda uku. Sai dai babu yanda aka iya da ƙaddara. Ma'aruff ya haɗiye abu mai nauyi daya tsaya masa a maƙoshi, tare da matsawa kusa da Lailah ya jawota jikinsa a karo na farko a rayuwarsu ya rungumeta. Sai kawai ta sake sakar masa kukan da yafi na farko. Murmurshi yayi mai ciwo. Kafin ya fara magana cikin ɗacin murya sai dai tana fita da sanyin sauti mai tafiya da lallashi...          “Yau rana ce ta farin ciki da ɗunbin tarihi a garemu, rana ce da iyayenmu sukaci buri a kanta damu kammu. Sai dai gata ta cika babu waɗanda mukema kallon iyaye na biyu a tare damu. Lailaty ƙaddara batai mana adalci ba, miyasa zata ɓoye mana su a lokacin da mukafi buƙatar su...?”       “Saboda makirci da zaluncin azzalumai ne Yaya Man. Kuma bazamu yafe musu ba..”      “Tabbas bazamu yafe musu ba Lailaty, za kuma mu cigaba da gayama UBANGIJI kukanmu da kai ƙararsu gareshi. Dan sun cutar damu.” hawayen da yake riƙewa suka shiga gangarowa suna sauka akan kafaɗarta. Da sauri ta ɗago tana kallonsa a karo na farko, sai ya kauda kai gefe yana murmurshi. “Bafa kuka nake ba, abu ne ya faɗa min a idona”.        Hannunta mai ɗauke da lallen da daƙyar suka yarda akai musu ita da Shariffa takai saman kyakkyawar fuskarsa mai kama data Ja'afar matuƙa, dan kamanninsu na saka mutane da yawa yarda su Twins ne. Fuskar ta maido saitin tata dan tabbatar da abinda ta gani, sai dai suna haɗa idon ya ɗaga mata gira kaɗan, cikin son kauda mata zargin dama yanayin nasu ya matsar da fuskar sosai gab da tata. Ƙoƙarin komawa baya tayi yay saurin riƙota ya hana hakan, nan ma tai ƙoƙarin kife kanta a kafaɗar tasa ya sake hanawa ta hanyar riƙo fuskar da duka hannayensa biyu, a bazata taji lips ɗinsa kan nata. Sai kawai jikinta ya kama rawa ta daburce, dan abunda batai zato ko tsammani bane daga garesa. Tun tana mutsu-mutsu harta nutsu dan tuni ya mannata da fuskar gadon dole ta sallama.      Sai da ya tabbatar ya tabbatar mata da wannan ranar da sun zama ɗaya ta hanyar sumbatarta yanda ya dace kafin ya haƙura. Gaba ɗaya kunya ta sanyata naɗewa a jikinsa tama kasa tashi. Shi ko murmushi kawai yake yana shafa bayanta. Yo banda ALLAH ya rage ma aya zaƙi ai wannan ranar tanadin da sukai mata shi da Ja'afar ɗinsa ba'a magana. Amma ina ƙaddara tace musu bata yarda ba, sai dai kawai ayi wani abun dan sauke haƙƙi da rahamar UBANGIJI mai sassauta zukatan bayi da ikonsa..........✍️ _Alhamdullahi barkanmu da dawowa a littafi na biyu. Duk da dai na barku da jira, Amin afuwa uzuri ne yasa aka samu dogon hutun. Ina fatan kuna cikin ƙoshin lafiya kuma bakuyi fushi ba 😘. Kar ku damu faka-faka ne in dai naga kuna so kuma. Dan in babu kwarin gwiwa daga gareku rubutun bazaiyi gudu ba kamar yanda muke fata. Karna cikaku da surutu kumuje zuwa kawai dan book 2 ɗin nan hummmm ba'a mana, in sha ALLAHU sai ya tashi kanku fiye da yanda kuke tsammani, na tattaro muku tari-tarin abubuwa a cikinsa da sai kun karanta kawai zaku gane abinda nake nufi 😘😘😘💃._ _Zaku sameshi a waɗan nan manhajar guda uku in sha ALLAHU._ *_NIGER🇳🇪- (500 CFA) (Telegram vip 1000 CFA)_* *_+227 98 94 12 81_* *_My NITA_* *_Zaku iya kuma tura katin Airtel na ƙasar NIGER shima 500 CFA ko vip telegram 1000 CFA_* _Shaidar biya👇_ *_Whatsapp number_* *_+227 98 94 12 81_* *_TELEGRAM VIP 1000 (1K)_* *9032345899* *_Moniepoint MFB_* *_BILKISU MUSA IBRAHIM_* *_KATI MTN (1k)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya: 👇_* *_Telegram Number 09032345899_* *_AREWABOOKS (Vvip)_* *_Chapters & Audio_* @BilynAbdull *_WHATSAPP (500)_* *1487616276* *_Access Bank_* *_Bilkisa Ibrahim Musa_* *_Kati MTN:- (500)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya:-_* *_Whatsapp Number +234 805 568 7449_* *_MASU SON A TALLATA MUSU KAYANSU SUMA_* *_WhatsApp Number 👇_* *+234 805 568 7449* *_Telegram Number👇_* *+234 903 234 5899* *_ASSALAMU ALAIKUM MUTANE NA MASU ALBARKA_* *_Maza ku matso MASOYAN Bilyn Abdull da IDANU suka hana karatun novels...._* *_Tofa Bilyn ku ta samo muku hanya mai sauƙi da kina aiki, ko kina kwance kina hutawa, ko kina inda baki son yawan surutu earpiece ɗinki kawai zaki maƙala a kunne ko Bluetooth kisha sauraren littafin KIƊA A RUWA.... Cikin sauƙi.... 💃_* *_Kar dai na cika ku da zance. Zamu fara saida littafin KIƊA A RUWA.... Na saurare (Audio) kenan akan farashi mai sauƙi da rahusa._* *_Akwai VVIP AREWAPEN kenan 💃_* *_Akwai VIP Telegram 💃_* *_(Ƴan WhatsApp ku haƙura kawai ƴan ta'addar bati sunfi yawa a cikinku gaskiya tsoron rashin m ɗinku nake 😂🤣)_* *_Telegram Audio 2k ne kacal ba tsada 💃. Sai kusaka ta wannan account ɗin👇_* _(2k)_ *9032345899* *_Moniepoint MFB_* *_BILKISU MUSA IBRAHIM_* *_KATI MTN (2k)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya: 👇_* *_Telegram Number 09032345899_* *_Ƴan NIGER🇳🇪 kuma bazamu barku a baya ba in sha ALLAHU zaku biya (Telegram vip 1,500 CFA) domin littafin KIƊA A RUWA..... na ji Audio-vocal. Sai ki biya tanan👇_*. _(1,500 CFA)_ *_+227 98 94 12 81_* *_My NITA_* *Zaku iya kuma tura katin Airtel na ƙasar NIGER shima 1,500 CFA vip telegram _Shaidar biya👇_ *_Whatsapp number_* *_+227 98 94 12 81_* *_AREWAPEN (Vvip)_* *_Chapters & Audio_* @BilynAbdull *_Ƴan WhatsApp kuzo muyi shawara idan zaku iya amana ayi harkar nan daku 😂, dan bana son a barku a baya duk da dai bakwa ji, ba raga min zakuyi ba na sani duk da ƙaunar da nake muku 🤣😂._* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* [01-16, 11:37] +234 703 449 6321: *_Typing📲_* *_💦KIƊA A RUWA...!!💦_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_GENERAL FICTION_* _Wannan labari ƙirƙirarre ne. Sunaye, wurare, da abubuwan da suka faru duk ƙirƙira ne, ba su da alaƙa da gaskiya ko wani, koda Bilyn Abdull ce 😂._ *_BOOK 2_* _Chapter 2_ __________________ _A KANO KI KE…? Kina neman inda zaki siyi abinci mai daɗi? Kina ƙiyar yin girki gashi zaki yi baƙi?, kina neman inda zaki yi order abinci mai daɗi wanda zaki fita kunya?. Masu abinci suna suka tara, akwai abinci mai daɗi akwai a lallaɓa. Kina son ki siyi abincin da zaki ɗauka a saudia ki ke? Kuna son ku siyi abincin da in kuna ci zaku dinga murmushi saboda daɗi da khamshi?. LEEMARS_DELICIOUS itace kat a wannan ɓangare, tazo muku da nau’in abinci kala-kala na gargajiya da na ƙasar waje. Tana siyar da MANDI RICE, GRILL CHICKEN, CHICKEN BIRYANI, FUNKASO, ALELEN GWANGWANI, BREAD POCKET da sauran su. Fannin abin sha akwai natural ZOƁO mai zaƙi, wanda aka yi shi da ingantattun kayan marmari masu ƙara lafiya, akwai wanda bashi da zaƙi domin masu ciwon sugar da masu gudun ƙiba._ _me ku ke jira? Maza ku garzaya shafin ta na instagram ko TikTok domin ku ganewa idanun ku, ku danna wannan link din domin yin magana da ita kai tsaye. Ko ku neme ta a number wayar ta da take ƙasan rubutun nan._ INSTAGRAM 👇🏻👇🏻👇🏻 https://www.instagram.com/leemars_delicious?igsh=MWRzZWtnYXM4ZHB2dw%3D%3D&utm_source=qr CALL/WHATSAPP 👇🏻👇🏻 wa.me/2349030398006 TIKTOK 👇🏻 https://www.tiktok.com/@leemars_delicious?_t=ZS-90ZQJ2mNJKc&_r=1 Kar ku sake a baku labari, siyan na gari mai da kuɗi gida.❤️❤️🫶🏻 __________________ *_TELEGRAM GROUP_* https://t.me/+erpSeN2ssqgwYTdk *_WHATSAPP CHANNEL_* https://whatsapp.com/channel/0029VbBMI7RLY6d9zU893c1F *_TIKTOK_* https://vt.tiktok.com/ZSDkPqMm1/ *_INSTAGRAM_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv ______________________ ..........Da ƙyar ya lallaɓata ta tashi tayo alwala, shima yayi suka gabatar da salla tare da addu'oi masu tsaho da rabinsu duk akan Yaya Imran da Dada ta ƙare. Bayan sun kammala ya riƙe hannunta, murya a sanyaye ya ce, “Yanzu ya za'ayi kenan?, ango na shigowa da kaza ni da Twiny na mun shigo hannu rabbana. Ina fatan aminan juna zasu yafe mana, amma in sha ALLAHU zamu biya wannan bashin ranar da kuka haifo mana Haysam da Imran”.          Murmurshi tayi tana mai sinne kanta saboda kunya. Shima sai ya sake murmusawa yana mai jawota jikinsa ya rungume gaba ɗaya yana sanya mata albarka. Cike da jin kunya tana naɗe a jikin nasa ta amsa da, “Amin na gode. In dai kaza ce mun yafe muku. Dan ko ma kun kawo bazamu ci ba”.        “Oh baki kuka haɗa kenan?”.    “A'a fa”. “Faɗi gaskiya dai Lailaty, dan gara mu sani, musan yanda zamu tafiyar da rayuwar aminan juna kada wata ran a haɗe mana kai a tare”.        Ƴar ƙaramar dariya tayi tana mai yunƙurawa zata bar jikinsa. Sai shima ya miƙe yana murmurshin da kamata ya ɗaga cak ya ƙarasa da ita zuwa gaban gadon. Zata janye ya hana hakan, sai ma ƙoƙarin warware lafaya ɗin jikinta da yake yi. Ba yanda ya iya kuma dole ta bashi dama yayi yanda yake so. Daga ƙarshe ya rikice mata dan rigace doguwa a ciki mai mannewa a jiki data fidda komai na halittar da UBANGIJI yayi mata masha ALLAH. Ita ko duk ta daburce saboda kunya, ƙoƙarin ganin ta ja lafayar ma ta fara dan rufe jikin nata. Amma ya hana hakan ta hanyar riƙe hannun nata yana shinshinar wuyanta dake fidda wani ƙamshi na musamman daga shiryayyun turarrukan SHUWA INCENSE AND MORE +234 704 229 3387 na musamman da aka shirya musu, dan hatta kayan gyaran jikin da akai musu duk daga gare ta ne. Abinka da tuzurun ango ji yay komai ya ƙwace masa. Tuni ya manta da batun bazasu iya taɓa amaren nasu ba anan kusa kamar yanda suke ayyanawa a zukatansu. Su kansu su Lailah sun sakankance angunan nasu zasu barsu sai nan gaba kodan halin da ake ciki, amma sai ga saɓanin haka, dan jikin Ma'aruff har rawa yake ya ɗagata cak zuwa gadon bayan ya sake manne lips ɗinsu tamkar ɗazun.....      ★Banbancin da aka samu tsakanin Ja'afar da Ma'aruff shine, shi da farko lallashin tashi gimbiyar Shariffa kawai yayi a farko. Ya mata nasiha akan muhimmancin haƙuri duk da shima nasihar kamar yana yinta ne harda kansa. Hannu yasa ya share mata hawayen da suka jiƙe fuskarta sannan ya kamata ya miƙar shima yana miƙewa. Kusancinsu ya sakata jin kunya sosai ta kasa daurewa ta duƙar da kanta tana kallon ƙafafunsu. Amma sai ya saka hannu ya ɗago fuskar tata ta hanyar kamo haɓarta. Cike da raɗa ya furta,          “Sherry kalleni mana”.     Kanta ta girgiza alamar a'a.   Ya sake ƙanƙance murya da matsar da fuskar tasa gab da tata ya ce, “Why?”.       “Ina jin kunya Yaya J”.    Ta bashi amsa hawayen da take riƙewa na silalowa a saman kyakkyawar fuskarta”.        A hankali ya haɗiye abinda ya tokare nasa maƙoshin, kafin ya sake matsota jikinsa da ƙyau ya rungumeta. Murya a shaƙe irin ta mai damuwa ya ce, “Kina son nima na miki kukan?”.       Kanta ta girgiza masa alamar a'a tana jan shashsheka. Ya fara ɗan buga bayanta kaɗan-kaɗan alamar lallashi, sannan ya cigaba da faɗin, “Kiyi haƙuri, ko nace muyi haƙuri. Haka ALLAH ya tsara komai bamu isa canjawa ba. Ki ƙarfafa ni Sherry dan nima gab nake da faɗuwa. Ina jin tamkar bamuyima Dada da Yaya Imran adalci ba a wannan ranar. Kamar mun fifita buƙatarmu akan halin da suke ciki. Kwanaki goma sha huɗu kacal da yanke musu hukuncin zalunci da bamu da tabbacin kuɓutarsu an ɗaura mana aure. Miyasa su Mammah suka kasa fahimta ne?”.       Kuka mai raɗaɗi Shariffat ta saki, dan kalamansa na fita tamkar yana karanta abinda ke cikin zuciyarta ne. Ita ƙanwar Aunty Hafsat ce, kuma cousin's suke da su Imran, hasalima a gidan su Imran aka riƙesu su biyar ciff sakamakon rasuwar mahaifinsu tun ita bata wuce shekara tara a duniya ba. Yanda su Ja'afar ke ɗaukar Imran Yayansu jininsu haka suma suke kallon Dada a garesu. Da ƙyar Ja'afar ya share nashi hawayen, ya fara lallashinta da daɗaɗan kalamai. Sannan ya kama hannunta zuwa bayi sukai alwala. Sun gabatar da salla da addu'oin da suma a nasu ɓangaren mafi rinjaye suka tafi akan Imran da Dada. Shine ya fara miƙewa, ya je wadrobe ya ɗauka mata kayan barci ya dawo inda take. Kamata yay ya miƙar yana faɗin, “Kukan ya isa haka, canja kaya dare na ƙara yi, ga kaina na ciwo ina son na kwanta”.      Hawayenta ta share, ta amshi kayan ta nufi hanyar bayi. Bai hanata ba ya kai zaune bakin gado. Da gaske kansa ciwo yake kamar zai faɗi, dan haka ya kai kwance kawai yana rage fitilar ɗakin. Fin mintuna goma sannan ta fito, idanunsa a lumshe dan motsinta kawai yake ji. Sai dai jin shiru babu alamar ta ƙaraso wajen gadon ya sashi buɗe idanun a hankali. A mamakinsa can ya hangota kan sofa ta kwanta. Ya ɗan murmusa da buɗe baki a hankali cikin murya mai taushi ya kira yi sunanta..        “Sherry!”.     Amsawa tai a ƙasan maƙoshi, sakamakon kuka daya disar mata da murya.      “Mi kike yi anan?”.   Tana faman cuɗa hannayenta a waje guda ta ce, “Zan kwanta ne”.      “Kuma anan?”. Kanta ta jinjina masa. Sai ya ɗan girgiza kai yana wani murmushin. Cike da lallashi ya ce, “Toyi haƙuri ki dawo nan. In dai nine babu abinda zai faru barci kawai zamuyi. Zoma kimin addu'a kaina ciwo yake sosai”.      Ciwon kai daya ambata ya sata tashi ba musu ta nufesa. Sai dai sai faman gyaran wuyan riga take duk da mai ƙwala ne bai kuma mata yawa ba. Hasalima kayan wando da riga ne sun mata burun-burun. Hannun daya miƙa mata alamar tazo ta side ɗin da yake ya sata nufar can. Zata zauna a side drawer ya riƙo hannunta dole ta zauna a bakin gadon kusa da shi har jikinsu na gogar na juna. A haka ya ɗaura hannunta saman goshinsa da sanyin sa ya sashi sakin ajiyar zuciya. Ita kuma ɗumin goshin ya ratsata. Baiyi magana ba itama batace komai ba ta fara masa addu'ar ciwon kai tana tofa masa da shafawa. Fin mintuna biyar ta kammala, tana masa sannu zata miƙe ya hanata, zatai magana ya ce, “Shiiii!” yana kamota gaba ɗayanta a haka ya hawo da ita gadon, maimakon ya barta ta kwanta a gefensa sai ya barta a jikinsa a haka yaja musu bargo dan akwai ɗan sanyi-sanyi.      Ina ƙasa Shariffa ta shige ko zata huta da kunyarsa. Ga zuciyarta nata bugawar tsoron da har yana iya ji. Har cikin rai bata tunanin wani abu zai faru, a ganinta halin da suke ciki akan su Dada ai basu da lokacin wani abu kuma a yanzu. Amma mi a bazata taji saukar hancinsa akan wuyanta yana bin ƙamshin turaren SHUWA INCENSE AND MORE +234 704 229 3387. Da aka zazzage musu kala-kala a jikin. Ga wanda akai musu gyaran jiki. Ga kabasa da akai musu turaren kaya. Ga khumra kusan kala uku da aka basu suka shafa, gana man gashi, ga oils. Hatta ƙanshin sashen duk turaren wutar SHUWA INCENSE AND MORE ne. Al'amarin kamar wasa ƙaramar magana ta zama babba, dan tana tunani kawai sai jin saukar lips ɗinsa tayi a cikin bakinta. Kafin tayi wani yunƙuri ya sake matseta yana yanda yaso. Da ƙyar ya iya raba lips ɗinsu yana faɗin, “Sherry wannan wane irin turare ne mai canja tunani da hana gangar jiki zama lafiya ya rabbi.”       Bai ma bari ta bashi amsa ba ya sake ɗaukar wani sabon salon mai gigitarwa, ai duk yanda yaso control ɗin kansa da batun damuwa da barinta ba yanzu ba shima a nashi ɓangaren lissafin ya canja gaba ɗaya. Dan kuwa dai mai afkuwa ta afku ya bar Sherry ɗin tasa da kuka da magiyar neman ceto. Sai dai a wannan gaɓar babu mai jinta balle ya kawo taimakon, kamar yanda babu mai jin kukan aminiyarta Lailatyn ya Ma'aruff dake can itama tana amsar sakamakon nata ƙamshin turaren.      Masu karatu sai ku gayama Maman Abdull kayanta sun haɗa yaƙin ƙasa da ƙasa. Tai maza ta kawo ɗaukin ruwan zafi inba haka ba mu tattaro mumu zuwa gidanta a bamu rabonmu. Koda yake nifa na riga na kama nawa rabon mutanena. Kuma ku garzaya ku amshi naku dan wlhy turarrukan nan ba ƙarya, ni shaida ce a kansu ƙwarai da gaske. Ba amare kawai ba har uwargida kina buƙatarsu kodan faranta ranki da ƙamshi, balle ma idan oga yaji shima fa zai iya rikiɗewa zuwa Yaya Ma'aruff da Yaya Ja'afar. SHUWA INCENSE AND MORE +234 704 229 3387. Suna da turare wuta da khumra kaloli har uku: black humra, white humra, brown humra. Akwai oil perfume da kullacham da genine da Turare kabasa kaloli uku shima. white, black, and brown. Akwai man kitso, da kayan gyaran jiki masu gyara fata da sanyata laushi da santsi kiyita glowing abinki hajjaju. Kar ku bari a yi babu ku, tana aika kaya a duk inda kake har wajen Nigeria makwaftanmu. Ga arha ga mutunta customers abin sai wanda ya gani. SHUWA INCENSE AND MORE +234 704 229 3387. Tabbaci ne na haƙiƙa daga ni Bilyn Abdull dan na gwada na tabbatar😘😘💃. Washe gari sai ga angunan da aka kora tsitt kake ji, suna can suna aikin lallashi da sanya albarka. Dan kuwa suma dai sun isa duniya mai tsada da sai ɗan gata ɗan ƙwarai ke zuwanta har ya zame masa tarihi a ranar farko. Babu abinda zasuce da UBANGIJI sai godiya. Tare da addu'a da fatan ALLAH ya fito musu da su Dada anan kusa dan farin cikinsu ya ƙara girma. Maman Abdull kam dole ne taci ƙyauta ta musamman...........✍️ _Zaku sameshi a waɗan nan manhajar guda uku in sha ALLAHU._ *_NIGER🇳🇪- (500 CFA) (Telegram vip 1000 CFA)_* *_+227 98 94 12 81_* *_My NITA_* *_Zaku iya kuma tura katin Airtel na ƙasar NIGER shima 500 CFA ko vip telegram 1000 CFA_* _Shaidar biya👇_ *_Whatsapp number_* *_+227 98 94 12 81_* *_TELEGRAM VIP 1000 (1K)_* *9032345899* *_Moniepoint MFB_* *_BILKISU MUSA IBRAHIM_* *_KATI MTN (1k)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya: 👇_* *_Telegram Number 09032345899_* *_AREWABOOKS (Vvip)_* *_Chapters & Audio_* @BilynAbdull *_WHATSAPP (500)_* *1487616276* *_Access Bank_* *_Bilkisa Ibrahim Musa_* *_Kati MTN:- (500)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya:-_* *_Whatsapp Number +234 805 568 7449_* *_MASU SON A TALLATA MUSU KAYANSU SUMA_* *_WhatsApp Number 👇_* *+234 805 568 7449* *_Telegram Number👇_* *+234 903 234 5899* *_ASSALAMU ALAIKUM MUTANE NA MASU ALBARKA_* *_Maza ku matso MASOYAN Bilyn Abdull da IDANU suka hana karatun novels...._* *_Tofa Bilyn ku ta samo muku hanya mai sauƙi da kina aiki, ko kina kwance kina hutawa, ko kina inda baki son yawan surutu earpiece ɗinki kawai zaki maƙala a kunne ko Bluetooth kisha sauraren littafin KIƊA A RUWA.... Cikin sauƙi.... 💃_* *_Kar dai na cika ku da zance. Zamu fara saida littafin KIƊA A RUWA.... Na saurare (Audio) kenan akan farashi mai sauƙi da rahusa._* *_Akwai VVIP AREWAPEN kenan 💃_* *_Akwai VIP Telegram 💃_* *_(Ƴan WhatsApp ku haƙura kawai ƴan ta'addar bati sunfi yawa a cikinku gaskiya tsoron rashin m ɗinku nake 😂🤣)_* *_Telegram Audio 2k ne kacal ba tsada 💃. Sai kusaka ta wannan account ɗin👇_* _(2k)_ *9032345899* *_Moniepoint MFB_* *_BILKISU MUSA IBRAHIM_* *_KATI MTN (2k)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya: 👇_* *_Telegram Number 09032345899_* *_Ƴan NIGER🇳🇪 kuma bazamu barku a baya ba in sha ALLAHU zaku biya (Telegram vip 1,500 CFA) domin littafin KIƊA A RUWA..... na ji Audio-vocal. Sai ki biya tanan👇_*. _(1,500 CFA)_ *_+227 98 94 12 81_* *_My NITA_* *Zaku iya kuma tura katin Airtel na ƙasar NIGER shima 1,500 CFA vip telegram _Shaidar biya👇_ *_Whatsapp number_* *_+227 98 94 12 81_* *_AREWAPEN (Vvip)_* *_Chapters & Audio_* @BilynAbdull *_Ƴan WhatsApp kuzo muyi shawara idan zaku iya amana ayi harkar nan daku 😂, dan bana son a barku a baya duk da dai bakwa ji, ba raga min zakuyi ba na sani duk da ƙaunar da nake muku 🤣😂._* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_*[01-16, 11:37] +234 703 449 6321: *_Typing📲_* *_💦KIƊA A RUWA...!!💦_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_GENERAL FICTION_* _Wannan labari ƙirƙirarre ne. Sunaye, wurare, da abubuwan da suka faru duk ƙirƙira ne, ba su da alaƙa da gaskiya ko wani, koda Bilyn Abdull ce 😂._ *_BOOK 2_* _Chapter 3_ __________________ *_MS TOFA GALLERY_* Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/D1ZOZr50SfwCQUbhMB0eVC CEO Maryam Tofa 07010346400 inshaAllah zakiyi dariya kayanmu nada sauki da inganci kedai kiyi joining group din don ganewa idonki kaya masu kyau da aminci. Akwai GHT Supplements masu inganci.Allah yasa damu da alkhairi. __________________ *_TELEGRAM GROUP_* https://t.me/+erpSeN2ssqgwYTdk *_WHATSAPP CHANNEL_* https://whatsapp.com/channel/0029VbBMI7RLY6d9zU893c1F *_TIKTOK_* https://vt.tiktok.com/ZSDkPqMm1/ *_INSTAGRAM_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv ______________________ ..........Itama dai Nabeeha tun da batun kama Zak-Shadow ya ɓulla hankalinta ya tashi, a lokacin suna umara ita da uwarta. Dan bayan tabar gidan da ita umara suka tafi ita da yaran kaf, wai first lady ce ta biya musu. Hankali tashe ta matsawa uwar suka dawo Nigeria, duk wani tsalle-tsallen tashin hankali da ita akayi sa, kamar abin arziƙi ta dawo gidai, sai dai ana fara bikin su Ja'afar mahaifiyarta ta janye ra'ayinta ta sake barin gidan ta koma gidanta ba'ai bikin da ita ba sam, daga baya kuma ta janyeta suka koma Dubai inda harkokinta sukafi yawa yanzu. Sai bayan da aka yanke ma su Dadan hukunci da fin wata uku ta ɗanzo ƙasar, shima basu wani jima ba ta sake komawa, acewarta bazata iya zama cikin tashin hankali da damuwar tuna Haysam na tsare ba, tsarewar da har lokacin an hana kowa ganinsa kusan shekara ɗaya. Tun daga nan data koma bata sake waiwayen ƙasar ba sai a 2016, sannan Zak-Shadow da Imran nada shekaru uku a gidan yari. A kuma lokacin ne aka saki Imran saboda kai-kawon da matasa suka cigaba da yi har lokacin batare da nuna gajiyawa ba, na Zak-Shadow ne dai yayi tsamari da yawa, shima kuma sunce bazasu sare ba zasu cigaba da gwagwarmaya...        A dalilin dagewar General Yusuf Shu'aibu... Na ganin an saki Dada kamar yanda aka saki Imran akai masa ritaya, dan kuwa ƙungiyar duhu sun fahimci shine ke tsaye kan matasan dake kai-kawo akan al'amarin Zak-Shadow da Imran ɗin, ga shi kuma sunci nasara akan fidda Imran saura Dada, dan haka sukai gaggawar sakawa a daƙileshi dan zuwa yanzu sunyi matuƙar jan hankalin ƴan siyasa a cikin tafiyar tasu fiye da zaton mai hasashe.      Satin Imran ɗaya da fitowa aka sauke General Yusuf Shu'aibu Tafida aka maye gurbinsa da wani. Wannan canji yayi matuƙar kawo ka-ce-na-ce da cecekuce a cikin ƙasa dama kafofin yaɗa labarai, sai dai gwamnati ta toshe kunnuwanta da yin kunnen uwar shegu da komai ta nuna babu gudu babu ja da baya. Bayan ɗaukar lokaci komai ya lafa dole ƴan ƙasa suka amshi sabon canji.        General Yusuf mai ritaya yaji zafin abinda ya faru, sai dai bai nuna ba ya shanye komai tare da komawa gefe kamar yanda akaso. Abu ɗaya ne bai haƙura da shi ba shine ganin Imran ya koma kan aikinsa, duk da shi a lokacin ya nuna baya buƙatar cigaba da aikin soja kuma. Amma Janar ɗin ya tsaya tsayin daka ya fahimtar da shi ammafanin cigaba da aikinsa ne kawai zasu samu taimakon fitowar Zak-Shadow batare daya cika shekaru ashirin da biyar ɗin da aka ɗiba masa ba. Jin haka yasa Imran yarda ya koma kan aiki duk da kuwa a lokacin watansa ɗaya kacal da fitowa a kurkuku...       Tabbas shawarar Janar tayi amfani, dan kuwa komawar Imran aiki ta bashi damar ganawa da Zak-Shadow a karo na farko. A lokacin daya samu umarnin samun wannan damar sai da hawaye suka zubo masa. Imran na matuƙar son Haysam, soyayya irin mara misali ɗin nan da UBANGIJI ne kawai mai tafiyar da ita a zukatan bayi batare da sun san taya take gudana ba......       >>><<•>><<<   21/11/2016          Ranar Litinin ƙarfe goma sha ɗaya na safe Imran ya nufi Special Military Corrections Facility, North Central Command Base inda Zak-Shadow yake. Rana ce da ta fi kowace rana nauyin da sanya zuciya zumuɗi da rauni a lokaci ɗaya a ƙirjin Major Imran Abbas.       A daren jiya bai runtsa ba tunda ya samu tabbacin amincewar zuwan nasa. Kai gaba ɗaya ma kasa zaune kasa tsaye yayi tun da yaga sakon janar mai ritaya ya shigo wayarsa _(An amince. Zaka iya ganin sa gobe. Imran kada ka yi wani abu da zai rikita zuciyarka wannan dama ce muka samu)_ Sai zuciyarsa ta tsaya cak tana mai tsitsinkewa, kai jikinsa kansa tsuma ya dinga yi har sai da Aunty Hafsat ta jeho masa tambaya. Amma sai bai iya bata amsa ba ya girgiza kai kawai. Shekaru uku kenan ba tare da yaga fuskar Haysam ba. Shekaru uku na tambayoyi, na tunani, na laifi da raɗaɗin rabuwa. Shekaru uku na jin kamar mutuwa mai yankewa ta yanke wannan alaƙar ta har abada. Zaman prison bai jikata zuciyarsa ba kamar tunanin halin da Haysam ke ciki. Cikin dabara ya kai hannu yana share guntayen hawayen da suka taru masa a gefen ido...      Washe gari tunda sassafe ya baro gidansa saboda tsabar zumuɗi, maimakon office kuwa kai tsaye Special Military Corrections Facility North Central Command Base ya wuce. Haka ya samu waje can nesa da prison ɗin ya tsaya zaman kusan awanni uku har lokacin da aka bashi ya cika sannan ya kunna motar ya karasa. A hankali motar sa ta tsaya a gaban babban ƙofar ƙaton gate ɗin. Tsaron wajen ya banbanta da duk wani waje da Imran ya taɓa gani, dan shi ba'a nan aka ajiye shi ba a nashi zaman. Birgedun sojoji biyu a wajen ƙofar, camaras a jikin bango, wasu guards suna sintiri cikin takun da ke nuna horo mai tsauri a wajen.       “Major Imran Abbas?” ɗaya daga cikin guards ɗin ya tambaya.    “Eh, ni ne”. Muryarsa ta yi nauyi kamar anyi masa sarƙa a wuya saboda yanda yake jin kansa da zuciyarsa dake bugawa da sauri-sauri.       “Follow me, sir.”    Kansa kawai ya jinjina, a ƙasan zuciyarsa yana ambaton sunan ALLAH. Ya bi guards ɗin zuwa wani dogon corridor da yake a tsaftace alamar ana kula da wajen sosai fiye da kima. Daga can suka kai shi wani ɗaki da shima yake zagaye da camaras kamar tsiya.      “Ka ajiye wallet, takardu, da belt. Za a bincika ka kafin a shiga.”     Babu wani nuna damuwa Imran ya cire belt ɗinsa dan wannan yasan dokar soja ce. Bai taɓa tunanin zai zo wannan wuri saboda Haysam ba. Bai taɓa hango cewa watarana ƙaddara zata kwaso su zuwa wannan ramin mai tudu da kwazazzabo ba.      Bayan an kammala bincike sa yanda ya dace suka fita a ɗakin, wani ƙaramin ɗakin ganawa suka kai shi, wanda ke da tebur biyu da gilashi tsakanin su. Amma shi an canja musu saboda matsayinsa daga shi har Zak-Shadow ɗin, dan haka aka basu ɗaki na musamman ba tare da gilashi tsakanin su ba.       Wani irin duka zuciyar Imran take tamkar ƙarfen agogo dake bada sakanni na motsawa ne da ita. Minti biyar.. Minti goma.. shiru. Sai zuciyar Imran ta ƙara ƙarfin bugawa kamar bugun gangar yaƙi, dan adadin mintinan da aka saka zai iya fitowa sun cika..       Dai dai nan kuwa aka buɗe ƙofa a hankali. Sojoji biyu suka shigo da Lt. Colonel Haysam Abdul-rasheed Shehu Kobi. Sai dai ba irin Zak-Shadow ɗin da duniya ta sani bane a baya. Wannan Zak-Shadow ɗin ya canja da canje-canje masu yawan gaske, musamman a suffa ta soja zuwa wani abu daban, gashinsa ya yi tsawo sosai sama da yadda yake da, fuskarsa ta ajiye saje saɓanin da da babu ko ɗigon gashi a fuskarsa saboda kasancewarsa soja, fuskar sa ta ɗan rame amma kwarijin da cikar kamalar da gizago zaratan MAZAJEN na nan shimfiɗe a kanta. Ga tambarin sallarsa ya sake fita baƙi sosai akan goshinsa saboda hasken zaman waje ɗaya da fatarsa ta sake yi, ainahin haskensa na da kafin wahalar soja ta dusar da shi ya sake bayyana. Idanun nan kam sun wani sake juyewa kamar na kumurcin maciji.      Hannunsa na sanye da ƙananan cuffs saboda dokar prison. Shi dama can bamai ƙiba bane, amma jikinsa a buɗe yake da ginannen ƙarfi irin na masu kulawa da tattali, dan haka ko a yanzu bazakace ya rame na tashin hankali ba, dan daga ganinsa kasan bai daina motsa jikin ba, zaka tabbatar da haka saboda takunsa dai nasa ne na soja mai ji da kansa, ko a cikin jeji, ko a cikin duhu. Ko a cikin bainar jama'a wannan takun ƙasaitar da jarumta baya canjawa.       Ya ɗan tsaya kafin ya zauna. Sai kuma ya kalli guards ɗin da juyayyun idanunsa ya kaɗa kai kaɗan. Su sun san nan ɗin ba wajen wargi bane, dan ko KURA TA RAME TAFI ƘARFIN WAWASON ƘANANUN NAMUN JEJI. Ga shi dai a tsare, amma takashi ko manyan KAYA sun gagara, shiyyasa a tsaren yake amma girmamawa babu abinda ya canja. Ai ko mahaukaci yasan kallon ZAKI sai daga nesa, a nesan ma daga bayan keji, dan ko hannu ya samu zai iya yin wawaso. Yafi ƙarfin kallon banza ma balle ace za'a dake shi. Fitar kuwa sukai da sauri suka barsu su kaɗai.       Shiru ya cika ɗakin. Shiru mai nauyin da ko ƙarar bindiga da harbi bai zama lallai ta iya yankesa ba. Su duka biyun sun zubama juna ido ne kawai kamar masu kallo a cinema. Imran ya ji hawaye sun cika masa ƙwayar ido. Amma ya danne. Zuciyarsa na ƙaraji. Dole ya kauda nasa idanun da kansa gefe yana ƙoƙarin haɗiye hawayen. Zak-Shadow ya ɗan girgiza kansa, tare da zama, a hankali ya jingina bayan sa da kujerar. Juyayyun idanunsa suka sauka a fuskar Imran daya sake juyowa kamar yana lissafa duk wani abu da bai faɗa masa ba shekaru uku da suka shuɗe.        Ganin Imran bashi da niyyar yin magana shi ya motsa nashi lips ɗin da sukai jazur cikin dakakkiyar golden voice ɗinsa dake cike da izza da amo ya furta, “Major Imran Abbas.”      Kalmomi uku ne kacal. Amma Imran ya jisu har cikin tsakiyar zuciyarsa da brain. Da ƙyar ya iya dauriyar amsa wa da.       “Sir…”    Muryarsa ta kasa fita gaba ɗaya saboda sabbin hawayen dake cika masa idanu.........✍️      😭😭😭😭😭😭🙏 _Zaku sameshi a waɗan nan manhajar guda uku in sha ALLAHU._ *_NIGER🇳🇪- (500 CFA) (Telegram vip 1000 CFA)_* *_+227 98 94 12 81_* *_My NITA_* *_Zaku iya kuma tura katin Airtel na ƙasar NIGER shima 500 CFA ko vip telegram 1000 CFA_* _Shaidar biya👇_ *_Whatsapp number_* *_+227 98 94 12 81_* *_TELEGRAM VIP 1000 (1K)_* *9032345899* *_Moniepoint MFB_* *_BILKISU MUSA IBRAHIM_* *_KATI MTN (1k)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya: 👇_* *_Telegram Number 09032345899_* *_AREWABOOKS (Vvip)_* *_Chapters & Audio_* @BilynAbdull *_WHATSAPP (500)_* *1487616276* *_Access Bank_* *_Bilkisa Ibrahim Musa_* *_Kati MTN:- (500)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya:-_* *_Whatsapp Number +234 805 568 7449_* *_MASU SON A TALLATA MUSU KAYANSU SUMA_* *_WhatsApp Number 👇_* *+234 805 568 7449* *_Telegram Number👇_* *+234 903 234 5899* *_ASSALAMU ALAIKUM MUTANE NA MASU ALBARKA_* *_Maza ku matso MASOYAN Bilyn Abdull da IDANU suka hana karatun novels...._* *_Tofa Bilyn ku ta samo muku hanya mai sauƙi da kina aiki, ko kina kwance kina hutawa, ko kina inda baki son yawan surutu earpiece ɗinki kawai zaki maƙala a kunne ko Bluetooth kisha sauraren littafin KIƊA A RUWA.... Cikin sauƙi.... 💃_* *_Kar dai na cika ku da zance. Zamu fara saida littafin KIƊA A RUWA.... Na saurare (Audio) kenan akan farashi mai sauƙi da rahusa._* *_Akwai VVIP AREWAPEN kenan 💃_* *_Akwai VIP Telegram 💃_* *_(Ƴan WhatsApp ku haƙura kawai ƴan ta'addar bati sunfi yawa a cikinku gaskiya tsoron rashin m ɗinku nake 😂🤣)_* *_Telegram Audio 2k ne kacal ba tsada 💃. Sai kusaka ta wannan account ɗin👇_* _(2k)_ *9032345899* *_Moniepoint MFB_* *_BILKISU MUSA IBRAHIM_* *_KATI MTN (2k)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya: 👇_* *_Telegram Number 09032345899_* *_Ƴan NIGER🇳🇪 kuma bazamu barku a baya ba in sha ALLAHU zaku biya (Telegram vip 1,500 CFA) domin littafin KIƊA A RUWA..... na ji Audio-vocal. Sai ki biya tanan👇_*. _(1,500 CFA)_ *_+227 98 94 12 81_* *_My NITA_* *Zaku iya kuma tura katin Airtel na ƙasar NIGER shima 1,500 CFA vip telegram _Shaidar biya👇_ *_Whatsapp number_* *_+227 98 94 12 81_* *_AREWAPEN (Vvip)_* *_Chapters & Audio_* @BilynAbdull *_Ƴan WhatsApp kuzo muyi shawara idan zaku iya amana ayi harkar nan daku 😂, dan bana son a barku a baya duk da dai bakwa ji, ba raga min zakuyi ba na sani duk da ƙaunar da nake muku 🤣😂._* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* [01-16, 11:37] +234 703 449 6321: *_Typing📲_* *_💦KIƊA A RUWA...!!💦_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_GENERAL FICTION_* _Wannan labari ƙirƙirarre ne. Sunaye, wurare, da abubuwan da suka faru duk ƙirƙira ne, ba su da alaƙa da gaskiya ko wani, koda Bilyn Abdull ce 😂._ *_BOOK 2_* _Chapter 4_ __________________ _A KANO KI KE…? Kina neman inda zaki siyi abinci mai daɗi? Kina ƙiyar yin girki gashi zaki yi baƙi?, kina neman inda zaki yi order abinci mai daɗi wanda zaki fita kunya?. Masu abinci suna suka tara, akwai abinci mai daɗi akwai a lallaɓa. Kina son ki siyi abincin da zaki ɗauka a saudia ki ke? Kuna son ku siyi abincin da in kuna ci zaku dinga murmushi saboda daɗi da khamshi?. LEEMARS_DELICIOUS itace kat a wannan ɓangare, tazo muku da nau’in abinci kala-kala na gargajiya da na ƙasar waje. Tana siyar da MANDI RICE, GRILL CHICKEN, CHICKEN BIRYANI, FUNKASO, ALELEN GWANGWANI, BREAD POCKET da sauran su. Fannin abin sha akwai natural ZOƁO mai zaƙi, wanda aka yi shi da ingantattun kayan marmari masu ƙara lafiya, akwai wanda bashi da zaƙi domin masu ciwon sugar da masu gudun ƙiba._ _me ku ke jira? Maza ku garzaya shafin ta na instagram ko TikTok domin ku ganewa idanun ku, ku danna wannan link din domin yin magana da ita kai tsaye. Ko ku neme ta a number wayar ta da take ƙasan rubutun nan._ INSTAGRAM 👇🏻👇🏻👇🏻 https://www.instagram.com/leemars_delicious?igsh=MWRzZWtnYXM4ZHB2dw%3D%3D&utm_source=qr CALL/WHATSAPP 👇🏻👇🏻 wa.me/2349030398006 TIKTOK 👇🏻 https://www.tiktok.com/@leemars_delicious?_t=ZS-90ZQJ2mNJKc&_r=1 Kar ku sake a baku labari, siyan na gari mai da kuɗi gida.❤️❤️🫶🏻 __________________ *_TELEGRAM GROUP_* https://t.me/+erpSeN2ssqgwYTdk *_WHATSAPP CHANNEL_* https://whatsapp.com/channel/0029VbBMI7RLY6d9zU893c1F *_TIKTOK_* https://vt.tiktok.com/ZSDkPqMm1/ *_INSTAGRAM_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv ______________________ ........Dada dake kallonsa kallo mai cike da ƙauna daga UBANGIJI ya ɗan ɗaga hannunsa yana masa Alamar ka tsaya ka nutsu. Sai kuma ya sake motsa lips ɗinsa kaɗan ya furta “You’re a soldier Imran… but seeing you like this is giving me a headache. What’s happening to you?why are you acting like a woman?”. Shima ya ɗan kawar da kansa gefe saboda idanunsa na son suyi wani abu saboda hawayen da suka sakko a fuskar Imran sharrrr. Kuka ko ɓacin rai ne shi kansa bai ma san wannene yake ji da ganin hawayen Imran ɗin ba. Cikin dakewarsa, idanunsa na kallon gefe ya sake furta, “Bazan tambayeka yaya kowa yake ba? Dan hakan shine mafi girman abinda zai sosa min ZUCIYA. Na ganka, shi ne abinda yafi komai muhimmanci Imran.”         Da ƙyar Imran ya tsaida hawayensa. Fuskarsa da murmurshin ƙarfin hali ya ɗan matsa gaba, hannayensa duk biyu ya ɗaura kan teburin. “Munyi ƙoƙari.. Munyi komai… amma suka zaɓi yimana wannan zaluncin Haysam…”       Dada ya katse shi da murya mai sanyi amma mai ƙarfi da nutsuwa, “Ba zalunci bane. Siyasa ce. Dama kuma ita siyasa ai ba ta rabuwa da jini.”      Kai Imran ya girgiza. Cikin son ƙarfafa kai ya ce, “Na fahimta, kenan sun kulle ka saboda sun tsorata. Sun tsorata da kai. Sun tsorata da gaskiya. Sun tsorata da abin da ka sani”.        “Na sani.”      Dada ya furta a hankali yana ɗan murmurshi. Shiru ya sake mamaye ɗakin kowa da abinda yake tunani, fin sakan goma ya maida kallonsa kan Imran kai tsaye, kallon da ya tattara shekara uku masu zurfi: jarunta, kewa, hikima, da raɗaɗin da ya gama zagaye zuciyar mutum daga mutum ta zama tamkar dutse.         Imran ya katse shirun da faɗin, “Kurakuraina suka kawo ka nan Haysam, zan sadaukar da rayuwata domin ganin ka fita kuma” ya share hawayen da suka sake silalo masa, batare daya bari yayi magana ba ya cigaba da faɗin, “Bayan rufe mu sun sauke COAS shima, sai dai bai daina gwagwarmaya ba, dan yanzu haka da tsayawarsa nazo nan.”        Idanu Dada ya lumshe a hankali, batare da kula zancen Imran na farko ba ya furta, “ALLAH ya saka masa da alkairi, dama nasan ba zasu barshi ba shi da duk masu goya mana baya. Imran… ka dawo min nan idan ka samu lokaci. Muna da magana mai tsawo. Kuma kada ka sake jin damuwa. Kai kaɗai ne wanda ban taɓa zargi ba.”       Idanun Imran suka sake zubo hawaye saboda wannan kalmomi na ƙarshe. Cikin jinjina kai ya ce, “Zak… har abada damuwa bazata barni ba in har kana a wannan wajen. Dan haka bazan taɓa barin ka a nan ba har abada”.        Dada ya yi murmushi. Ba mai annuri ko farin ciki ba. Murmushi ne kawai irin na jarumta da taurin zuciya. Shi yasan fitarsa a wannan wajen sai wani ikon ALLAH, amma ba abune mai sauƙi ba.       “Karka damu Imran. Ina a nan ne. Amma ba zan tsaya nan ɗin ba kamar yanda ƙaramin tunaninsu ke basu”. Sai ya jingina da kujera yana ɗan lumshe ido. “Kamar yanda na gaya maka kai ƙoƙari ka dawo. Idan ba haka ba ka fara zargina da guduwa, dan babu gudu babu ja da baya sai na ƙarasa wannan aikin”.        Tabbas Imran ya tabbatar da alwashinsa cikin idanunsa da suka sake rikicewa, ya kuma san wanene Zak-Shadow ɗinsa, kaɗan daga aikinsa ya aikata dukkan abinda ya ƙudurta. Zama ya gyara cikin sassauta murya dan baya son akai ga matakin da Haysam ke harin saboda komai zai sake jagulewa ne.       “Dan ALLAH kar akai ga haka MAZAN FAMA. Ina sha ALLAHU zan dawo. Zan dawo duk rintsi, zan......”        Motsin buɗe ƙofar da ake yi ya katse Imran. Sojojin ɗazun ne suka dawo, hakan ya sasu fahimtar lokaci ya cika. Dan haka kafin ma suyi magana Dada ya miƙe abinsa, sai kuma ya ɗan zubama Imran ido na sakan ɗaya, kafin cikin dakakkiyar muryarsa ya furta, “Imran…”      Imran ya ɗago kai yana kallonsa fuskarsa cike da damuwa da kewa..           Ƙaramin murmushi yay masa, tare da furta, “Ka tsare min kanka. Daga yanzu ka saka a ranka sabuwar ƙaddara ta fara motsi.” Daga haka ya juya abinsa yay gaba, ya bar Imran cikin shiru mai nauyin da bin bayansu da kallo, idanunsa cike da hawaye, dan a wannan ƙadamin yama manta da kansa a matsayin soja.......       <<>><<>><<>><<>>       Da ƙyar Imran ya iya jarumtar hana kansa sanarma su Mammah ganawa da Dada da yayi. Dan ya tabbatar zai saka musu sabuwar damuwa ne bayan sanyaya zukatansu da UBANGIJI yayi badan sun manta da damuwarsu ba tsahon shekara uku da wasu watanni. Amma kamar yanda Dada ya roƙesa kada yay masa zancen kowa saboda zai zama fami a zuciyarsa yasan suma a garesu haka ne. Sai kawai ya zaɓi yin shiru ko Aunty Hafsat matarsa bai gayama komai ba.        Hatta Janar dake jiran jin ta bakinsa ya gagara ganawa da shi. Dan a wani irin cinkushe zuciyarsa take a gaba ɗaya satin. Cikin kwanaki uku kacal bayan ganawar ta su rayuwar Major Imran Abbas ta canza. Ba ci, ba barci, sai tunanin kalamomin Zak-Shadow da yadda suka tsaya masa a wuya kamar an daure zuciyarsa da igiya. Duk inda ya zauna shi ne kawai a gabansa. Hatta aikinsa ya samu rauni a kwanakin nan.        Ranar alhamis karfe biyu na rana yake cikin ofishinsa shi kaɗai, ya na kallon rubutun bayanin da ya yi wa janar mai ritaya jiya. Dan ya yanke shawarar tunkararsa kawai a yau su tattauna yanda ya kamata. Kamar abin almara dai-dai lokacin wayarsa ta fara tsuwwa, sunan da yaga yana yawo a screen ɗin ya sashi kasa ɗagawa har sai da ta tsinke, sake kira na biyu ne ya maidoshi a hayyacinsa, ya sauke numfashi mai nauyi kafin ya ɗauki wayar yakai kunnensa. Cike da girmamawa yay sallama, tare da miƙa gaisuwa.      Daga can General Yusuf ya amsa, cikin damuwa ya cigaba da faɗin, “Imran kana lafiya kuwa? Kwanaki uku kenan ina saka ran ganinka amma shiru?”.        “Kayi haƙuri Sir kawai ina cikin ruɗani ne. Amma dama yau na shirya samunka a gida bayan na tashi aiki”.      Cikin sauke ajiyar zuciya Janar ya ce, “Nasan hakan zata faru, amma yaya zamuyi sai haƙuri Imran. In sha ALLAH watarana sai labari, duk wuya da juyin juya halin da za'ai Haysam bazai wulaƙanta ba da iznin UBANGIJI. Kazo dan nima na matsu mu tattauna”.         “In sha ALLAHU Sir zan zo”.    Daga haka sukai sallama Imran ya ajiye wayar.        ★Kamar yanda Imran yay alƙawari yana barin office gidan tsohon General Yusuf Shu'aibu Tafida ya nufa dake tsaftatacciyar anguwa. Sai dai sai da ya kira Aunty Hafsat ya sanar mata yau bazai shigo gida da wuri ba. Hayaniyar da yaji yake tambayarta “lafiya nake jin hayaniya haka?”.      Ta ce, “Lafiya lau mutanenka ne. Kaima kasan idan Nimrah da Ruƙayya na nan bakin kowa baya shiru. Daga Islamiyya suka zarto nan wai sai ka dawo ka maidasu gida”.          Murmushi yayi da girgiza kansa, zuciyarsa na ayyana masa ‘ai dama sai hali yazo ɗaya ake abota’ dan rashin jin da Nimrah da Ruƙayya ke zubawa abin har ba'a magana. Tuni sun koma masu gida biyu, basu gidan Mammah basu nan gidansa. A fili kam sai ya ce, “In dai banan zasu kwana ba ki kira Ammar ya ɗaukesu, dan nikam ba yanzu zan shigo ba. Kin san kuma Mammah bata ƙaunar suyi dare a waje”.       Cikin girmamawa tace, “Bari na kira shi to dan sunce komawa zasuyi. ALLAH ya dawo dakai lafiya”.      Da Amin ya amsa mata yana yanke wayar. Dai-dai kuma isowarsa babban gate ɗin gidan General Yusuf. Yay horn maigadi ya buɗe masa bayan ya leƙo yaga waye. Kasancewar ba yau ya fara zuwa ba, kuma maigidan ya sanar da zuwan nashi yasa aka buɗe masa gate ɗin kai tsaye. Yana gama parking ɗaya a cikin sojojin dake gidan yay masa rakkiya har babban falon General Yusuf kai tsaye, dan ba'a ajiye shi a falon baƙi ba ma.      Tunda ya shigo Genaral ke murmushi, Imran ya kai zaune cikin kujera shima tashi fuskar da ƙaramin murmushi. Gaisuwa yay masa irin ta oga kuma uba. Dan Genaral ya girmesu sosai a ƙalla yakai shekara 69 a duniya. Suko yanzu ne ma suka haura arba'in ɗin da wani abu. General ya amsa masa da kulawa, dan har cikin zuciyarsa yake jin ƙaunar Haysam da Imran saboda kwazon su da sanin aiki da gaskiya..        “Bismilah ga ruwa nan, ka kuma tashi muje muci abinci”.     Imran ya ɗan sake murmusawa yana shafa kai, cike da girmamawa ya ce, “Sir zan sha ruwan dai, abinci kuwa amin afuwa kada madam tayi fushi nabar nata”.       Ƙaramar dariya Genaral yayi duk da kuwa shima ba mutum ne mai yawan fara'a ba. Cike da dattako ya ce, “Gaskiya bazan so ɗiyata kam tai fushi ba. Amma duk da haka sai kaci, dan na saka an shirya maka ne na musamman”.     Babu yanda Imran ya iya dole ya haƙura suka hau teburin cin abincin da aka cika da kayan daɗi. Sai da suka fara cin abincin cikin nutsuwa falon shiru janar ya katse shirun da faɗin, “Ina fatan babu wata damuwa tare da Haysam? Yana cikin ƙoshin kafiya?”.        Sai da Imran ya haɗiye abincin bakinsa sannan ya jinjina kansa, sai dai fuskarsa ta janza zuwa damuwa. “Alhamdullih Sir. Babu wata bayananniyar damuwa ta zahiri. Dama kuma mun san bayan killacewa babu abinda zai yarda ya ɗauka ga wani na ƙasƙanci in dai Haysam ne. Dan har yanzu JININ MAZA na'a kan FARCE”.       Sosai Janar yay murmurshi mai faɗi. Ya ɗauki ruwa yana tsiyayawa a kofin gilashi. “Wato Imran da ƙasar nan tasan asarar da tayi na killace Haysam na kwana ɗaya kawai data jima da yima kanta da kanta ALLAH ya isa. Balle ma ace na tsawon shekaru uku da wasu watanni. Irinsu Haysam a ƙasa tamkar hasken diamond ne a tsakiyar sahara. Amma ban san miyasa ba, maimakon aga haskensu anfi kallon wahalar ɗakkosu da gujewa zafin saharar ne da yawanta..”         “Sir bazasu fahimta ba, irinku ƙalilanne ke fahimta saboda zukata masu ƙyau da ALLAH ya baku. Amma wlhy a tsayin rayuwata ban taɓa cin karo da mutum mai tsananin kishin ƙasa da son cigabanta ba irin Haysam. Mutum ne shi mara tsoro, mai tsayawa akan gaskiyarsa koda kuwa ace zata ƙona shi. Sannan yana so da sauri, shiyyasa yake komai da sauri. Amma na rasa miya tare musu?”........✍️ _Zaku sameshi a waɗan nan manhajar guda uku in sha ALLAHU._ *_NIGER🇳🇪- (500 CFA) (Telegram vip 1000 CFA)_* *_+227 98 94 12 81_* *_My NITA_* *_Zaku iya kuma tura katin Airtel na ƙasar NIGER shima 500 CFA ko vip telegram 1000 CFA_* _Shaidar biya👇_ *_Whatsapp number_* *_+227 98 94 12 81_* *_TELEGRAM VIP 1000 (1K)_* *9032345899* *_Moniepoint MFB_* *_BILKISU MUSA IBRAHIM_* *_KATI MTN (1k)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya: 👇_* *_Telegram Number 09032345899_* *_AREWABOOKS (Vvip)_* *_Chapters & Audio_* @BilynAbdull *_WHATSAPP (500)_* *1487616276* *_Access Bank_* *_Bilkisa Ibrahim Musa_* *_Kati MTN:- (500)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya:-_* *_Whatsapp Number +234 805 568 7449_* *_MASU SON A TALLATA MUSU KAYANSU SUMA_* *_WhatsApp Number 👇_* *+234 805 568 7449* *_Telegram Number👇_* *+234 903 234 5899* *_ASSALAMU ALAIKUM MUTANE NA MASU ALBARKA_* *_Maza ku matso MASOYAN Bilyn Abdull da IDANU suka hana karatun novels...._* *_Tofa Bilyn ku ta samo muku hanya mai sauƙi da kina aiki, ko kina kwance kina hutawa, ko kina inda baki son yawan surutu earpiece ɗinki kawai zaki maƙala a kunne ko Bluetooth kisha sauraren littafin KIƊA A RUWA.... Cikin sauƙi.... 💃_* *_Kar dai na cika ku da zance. Zamu fara saida littafin KIƊA A RUWA.... Na saurare (Audio) kenan akan farashi mai sauƙi da rahusa._* *_Akwai VVIP AREWAPEN kenan 💃_* *_Akwai VIP Telegram 💃_* *_(Ƴan WhatsApp ku haƙura kawai ƴan ta'addar bati sunfi yawa a cikinku gaskiya tsoron rashin m ɗinku nake 😂🤣)_* *_Telegram Audio 2k ne kacal ba tsada 💃. Sai kusaka ta wannan account ɗin👇_* _(2k)_ *9032345899* *_Moniepoint MFB_* *_BILKISU MUSA IBRAHIM_* *_KATI MTN (2k)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya: 👇_* *_Telegram Number 09032345899_* *_Ƴan NIGER🇳🇪 kuma bazamu barku a baya ba in sha ALLAHU zaku biya (Telegram vip 1,500 CFA) domin littafin KIƊA A RUWA..... na ji Audio-vocal. Sai ki biya tanan👇_*. _(1,500 CFA)_ *_+227 98 94 12 81_* *_My NITA_* *Zaku iya kuma tura katin Airtel na ƙasar NIGER shima 1,500 CFA vip telegram _Shaidar biya👇_ *_Whatsapp number_* *_+227 98 94 12 81_* *_AREWAPEN (Vvip)_* *_Chapters & Audio_* @BilynAbdull *_Ƴan WhatsApp kuzo muyi shawara idan zaku iya amana ayi harkar nan daku 😂, dan bana son a barku a baya duk da dai bakwa ji, ba raga min zakuyi ba na sani duk da ƙaunar da nake muku 🤣😂._* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_**_Typing📲_* *_💦KIƊA A RUWA...!!💦_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_GENERAL FICTION_* _Wannan labari ƙirƙirarre ne. Sunaye, wurare, da abubuwan da suka faru duk ƙirƙira ne, ba su da alaƙa da gaskiya ko wani, koda Bilyn Abdull ce 😂._ *_BOOK 2_* _Chapter 5_ __________________ *_MS TOFA GALLERY_* Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/D1ZOZr50SfwCQUbhMB0eVC CEO Maryam Tofa 07010346400 inshaAllah zakiyi dariya kayanmu nada sauki da inganci kedai kiyi joining group din don ganewa idonki kaya masu kyau da aminci. Akwai GHT Supplements masu inganci.Allah yasa damu da alkhairi. __________________ *_TELEGRAM GROUP_* https://t.me/+erpSeN2ssqgwYTdk *_WHATSAPP CHANNEL_* https://whatsapp.com/channel/0029VbBMI7RLY6d9zU893c1F *_TIKTOK_* https://vt.tiktok.com/ZSDkPqMm1/ *_INSTAGRAM_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv ______________________ .........“Bai tare musu komai ba, gaskiyarsa da rashin tsoro yasa suka kasance su a tsoracen. Sannan an tasirantar da siyasa ne a cikin al'amarin a yanzu.”           “Shima abinda ya gaya min kenan, da nace masa zaluncine yasa suka rufemu. Yace ba zalunci bane siyasa ce kawai”.      “Ƙwarai da gaske maganarsa gaskiya ce, wasan ya canja daga yanda ya fara ya koma siyasa saboda an janyo hankalin wasu masu zuciyar kwaɗayi a cikinsu da kuɗi, sannan duk masu son ayi gaskiya an daƙilesu. Kaga dai sunyi duk yanda zasuyi sun hana wasu a cikin adalan shugabanin komawa tenure ɗinsu ta biyu, sun ƙalama ministoci da yawa sharrin da sai da suka bar ƙasar. Yanzu sun ɗora wanda suke so akai gashi har sun shiga shekara ta uku akan mulki, sun samu damar yin yanda suke so. Duk da lafawar hare-haren nan dakaga an samu akwai manufar da suke son cimmawa ne kawai, sannan sun sami abinda suke so wato cigaba da haƙar ma'adanai.”         “ALLAH zai mana maganinsu Sir”.      “In sha ALLAHU Imran, sai dai muma dolene mu tashi tsaye sannan ne zamu samu taimakon UBANGIJI. Dan tabbas in dai ba wani motsi mai girma mukai ba akwai babbar matsala da zata iya faruwa anan gaba. Ciki kuwa harda halaka Haysam dana samu tabbacin suna shirin yi.”      Cikin matsanancin tashin hankali Imran ke kallon General. Shima sai ya jinjina masa kan nasa. “In sha ALLAHU bazasu samu dama ba. Shiyasa ma na yanke wani hukunci. Wanda ta hanyarsa ne kawai naga mafita a fitowar Haysam daga prison”.         Imran ya ture plate ɗin abincinsa gefe, cikin bugun zuciya da rawar murya ya ce, “Sir wane irin hukunci ne wannan? Wlhy komai wahalarsa da haɗarinsa zan kasance tare dakai muyi domin kuɓutar da Haysam, dan raina fansa akan Haysam Abdul-rasheed Shehu”.            Cikin jinjina kai da sauke ajiyar zuciya General ya ce, “In sha ALLAHU wannan abotar taku sai kunci moriyarta mai tsaho a duniya sannan ku kasance a aljanna tare. Imran a yanzu kaf hanyoyin fitar da Haysam na bisu amma duk an rufe su ta hanyar makirci da ƙarfin ikon masu mulki. Dan haka nai nazari nima da gane hanya ɗaya muma ta rage mana. Wato irin hanyar da sukabi suka rufe kaf ƙofofin muma dole ne mubi tanan mu buɗe ƙofifin. Dan tabbas Haysam shine ƙashin bayan karya waɗan nan mutanen da shirye-shiryen su. Badan wasu bazasu iya bane, badan babu kamar Haysam bane, badan babu masu irin gaskiyarsa da jarumtarsa bane. Akwaisu da yawa cikin matasan sojojinmu dama sa'anninku ɗin, kai harma wanda suka fishi duk za'a samu. Kawai Haysam shine ya fara musu illa, yay musu sani na haƙiƙa, sannan yake firgitasu da basu tsoro tunda har suka tattara duk karfinsu wajen son ganin sun danne shi. Dan haka ina son shi daya fara wannan aikin ya ƙarasa shi dan su san ZAKARAN DA ALLAH YA NUFA DA CARA...... Sannan da gaske shi ɗin KIƊA A RUWA NE MAI TADA HANKALIN SU. Dan haka Imran zan shiga SIYASA..”          “SIYASA! Sir?!”.     “Ƙwarai kuwa Imran SIYASA. Dan yanzu haka na fara shiga jikinsu, har wasu a cikinsu sun ɗorani a shawarar fitowa ɗan majalisan tarayya. Na kuma yarda na amince musu, sannan zan musu duk yanda suke so dan babbar kujerar mai gaba ɗaya nake hari nan da shekaru huɗu masu zagayowa bayan an gama tenure mai zuwa bayan wannan”.        “Turƙashi”. Cewar Imran yana zuba tagumi da hannu biyu. Murmurshi Genaral yayi mai faɗi, cike da dattako ya ce, “Yaƙin namu ne mu duka. Wannan shine hikimata ta cewa kada ka ajiye aikinka. Dan a yanzu haka kaima suna shirye-shiryen ƙara maka girma. Acewarsu zasu fara jan ra'ayinka dan zafafa zuciyar Haysam da ɗarsa masa cewar baka tare da shi. Su kuma samu sirrikansa....”       “ALLAH ya kiyaye, bana buƙatar ƙarin girmansu....”     Ƙaramar dariya Genaral yayi, cikin katse Imran ya ce, “Kwantar min da hankalinka mazan fama. A yanzu da bamu da zaɓin daya wuce maida kammu sakarkaru. Ta haka ne kawai zamu kamo bakin zaren, mu kuma tantance su waye ainahin munafukan. Su waye masu gaskiyar? Sannan mu cimma burin mu kuma. Amma na baka dama kaje kai tunani mai zurfi. Sannan zan sake shiga da fita dan ka sake ganawa da Haysam a karo na biyu, ka nema shawara a wajensa kuma. Imran idan wani zai iya gane zuciyar Haysam daga cikin duhun prison, kai ne. Ka koma. This time, ka saurare shi da idon zuciya, ka kuma gaya masa shirin mu da manufar mu. Na tabbatar zai bamu goyon baya shima.”            Wannan maganar ta General Yusuf ita ta kulle ma Imran baki tun jiya. Haka kuma ya cigaba da yawo da ita tsakanin safiya zuwa marece na kowane rana. Har ALLAH yasa a karo na biyu ya sake samun damar ziyartar Zak-Shadow a karo na biyu bisa tsayawar Janar ɗin...... <<•>><<•>>•<<>>        A PRISON GATE...       Ranar ta yi zafi sosai kasancewar ya tareta ne a lokacin zafin nata. Domin kuwa ƙarfe ɗaya ne a lokacin. Dan daga massalaci ma ya wuce special Military Corrections Facility.... ɗin. Wani nauyi ya lulluɓe zuciyar Imran tun daga lokacin da ya taka ƙasa ya ƙarasa gaɓar ƙofar babban prison ɗin. A karo na biyu cikin satittika biyu yana zuwa wurin da rabin zuciyarsa ke tsare.       Ya shigar da sunansa kamar zuwan farko, aka tabbatar da izinin shigarsa bisa doka. Daga haka aka rakashi zuwa ɗakin ganawar kamar na wancan lokacin. Wurin nan buɗaɗɗe da babu shamakin gilashi a tsakaninsu kamar saura, kujera biyu, teburi a tsakiya. Cikin mintuna kaɗan aka kawo Dada. Hannayensa daure da handcuffs, fuskarsa ɗin nan a ɗaure kamar yanda kowa ya santa, sai dai a yanzu babu zafafawa kuma ba murmushi. Amma idanunsa sun kasa ɓoye gajiyar shekaru uku da wahalar ƙuncin rashin aikin daya zamewa jiki da zuciya sabo.        Imran ya zuba masa ido batare da yace komai ba. Shi ma Dada bai yi magana ba har sai yada ya zauna. Sai wani ɗan shiru mai zurfi ya cika ɗakin. A hankali Dada ya zubama Imran ɗin juyayyun idanunsa, kamar yanda shima Imran ɗin ke kallonsa.      “Ni karka cinye ni”.    Dada ya faɗa yana hararar Imran. Murmurshi Imran yayi a karo na farko. Shima sai ya furta, “Da zaka haɗiyun ma ai da na huta. Kaga sai mu fice abinmu batare da kowa yaji ya gani ba mu koma gida kaga yanda Mammah ta ƙara ƙyawu. Nimrah da Ruƙayya dasu Asma'u da Khalifanka suka girma. Ma'aruff da Ja'afar suka zama magidanta harda ƙyawawan yara masu kama da kai da duk suka ci sunanka da sunana. Ammar da Bilal suka sake girma. Mu'azz ma ya fara zama ɗan saurayi. Ummi da Momy da Mimi sun sake haihuwa, Biebah ta sake zama budurwa ƴar jami'a. Nabeeha na cikin kewa da son ganinka.”       Wani sassanyan murmushi Dada yayi yana mai girgiza kansa da sake tsatstsare Imran ɗin da idanunsa. “Shike nan ka faɗa kaji daɗi, ALLAH ya albarkaci rayuwarsu gaba ɗaya. Ya sanya farin ciki da kwanciyar hankali a ciki. Ina fatan Mammah bata da wata damuwa?”.           Shima cikin murmurshi Imran ya ce, “Alhamdullahi Mammah na cikin ƙoshin lafiya. Duk da dai an shiga ruɗani a farkon ƙaddarar, amma zuwa yanzu zuciya ta amsa da hannu biyu kuma ALLAH ya saka nustuwa da farin ciki. Sai dai addu'a ba'a gajiya ba. Dan kwanan nan ma suka dawo daga Umrah su dukansu dan har Nimrah da Ruƙayya ba'a bari ba. Kasan yanzu sune autocin Mammah, suna zuba shagwaɓar su yanda suke so da rashin ji. Dan a wata biyu kawai da tawa dawowar an gayyaceni makarantarsu karo na huɗu kenan akan rashin jin su. Mammah kuma da anyi magana ta tare ko ina ta hana ai musu faɗa. Koda yake suma su Ja'afar ɗin babu mai son musu faɗan, sai Hafsa ce ma ke ɗan lallasasu idan sunje gidan shiyaysa basa son zuwa can su kwana”.         A mamakin Imran murmushi mai faɗi Dada yayi a yanzu fiye dana farko har haƙoransa na bayyana. Ya ɗan taɓe baki da faɗin, “Ai nasan za'a rina. Dan tun a ranar farko na fahimci kam hali yazo ɗaya. Shike nan dai Mammah ta cika min burina na ƙwace Ruƙayya.”       Imran ya ɗan murmusa shima da faɗin, “Ta cika maka kam ita da Nimrah, dan Nimrah ta taka rawar gani wajen janye hankalinta da ƙyau”.        “ALLAH ya raya su”. Ya faɗa a taƙaice.    Imran ya lumshe ido, muryarsa a raunane ya ce, “Amin ya rabbi. Gani na dawo Zak.... Ina bukatar ka bani dama dan fahimtar abin da bakace ba a ranar farko.”         Dada ya ja dogon numfashi. Ya jingina da kujera kamar mai yaki da wani abu a zuciya. “Babu abin da zan iya faɗa da baki ba tare da ya cutar dani ko ya cutar da ku ba”.      Imran ya jinjina kai. “Na fahimta, amma ka sani nazo jin duk abinda zaka iya rubutawa… Sannan a wannan gaɓar faɗar tafi amfani, dan nima ina tafe da muhimmiyar magana. Idan ba yau ba, yaushe?”         “Haka ne”. Cewar Dada yana zaro wasu murɗaɗɗun takardu daga ƙarƙashin rigarsa ta prison. Kai tsaye ya miƙa takardar ga Imran kamar yana mika zuciyarsa. “Ka sakata a jikinka dan nasan bazasu bari ka fita da ita ba. Na rubuta wannan cikin shekaru uku. Babu kuma wanda ya kamata ya gani sai kai.”       Hannu Imran ya miƙa masa shima, bai karɓa nan take ba saboda nauyin da kalmar “Sai kai” ta yi masa. Idanun Dada suna cike da gajiya amma akwai hasken wanda ya tsaya tsayin daka, wanda bai fasa ba, baya jin kuma zai fasa ɗin koda na daƙiƙa guda ne, duk da cin zarafi, yaƙi, da shekaru uku na shiru sukazo masa da shi. Ba wanda suka killacesa anan yake kallo ba ƘASAR da masu tasowa a GOBEN ƘASAR kawai yake hange da kallo. Shiyyasa ya yarda zai sadaukar wajen ginawa tare da duk mai zuciya irin tasa, domin ƴaƴa da jikoki su amfana a bayan rayuwarsu.        Imran ya karɓi takardar cikin sauke ajiyar numfashi. Kallonta yake cike da nauyi saboda sirrikan dake cikinta. Yana buɗewa ya ga layuka marasa yawa amma masu nauyi: Sunaye. Abubuwan da suka faru. Kurakurai. Shakku. Hujjoji. Da kalma guda ta ƙarshe. Sai kawai ya nannaɗeta kamar yanda ya bashi ya ɗaga rigarsa ya sakata a cikin ɗammararsa ta soja.        Imran ya haɗiye wani abu mai zafi da ya tsaya masa a makoshi. Cikin ɗacin murya ya ce, “Zak… me kake so mu fara? Ina kake so mu fara kalla ko tunkara?”.      Dada ya ɗaga kai ya kalle shi kai tsaye. Wannan kallo Imran bai taba mantawa da shi ba tun lokacin da suka yi fice-ficen yaki tare. Muryar jarumta ta shiga kunensa da izza da tabbacin MAZAN SUNA NAN A MAZANSU NA FAMA. GWARAZA KUMA BARADAI Masu tsayayyar zuciya da tsayayyar KALAMA..........✍️ _Zaku sameshi a waɗan nan manhajar guda uku in sha ALLAHU._ *_NIGER🇳🇪- (500 CFA) (Telegram vip 1000 CFA)_* *_+227 98 94 12 81_* *_My NITA_* *_Zaku iya kuma tura katin Airtel na ƙasar NIGER shima 500 CFA ko vip telegram 1000 CFA_* _Shaidar biya👇_ *_Whatsapp number_* *_+227 98 94 12 81_* *_TELEGRAM VIP 1000 (1K)_* *9032345899* *_Moniepoint MFB_* *_BILKISU MUSA IBRAHIM_* *_KATI MTN (1k)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya: 👇_* *_Telegram Number 09032345899_* *_AREWABOOKS (Vvip)_* *_Chapters & Audio_* @BilynAbdull *_WHATSAPP (500)_* *1487616276* *_Access Bank_* *_Bilkisa Ibrahim Musa_* *_Kati MTN:- (500)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya:-_* *_Whatsapp Number +234 805 568 7449_* *_MASU SON A TALLATA MUSU KAYANSU SUMA_* *_WhatsApp Number 👇_* *+234 805 568 7449* *_Telegram Number👇_* *+234 903 234 5899* *_ASSALAMU ALAIKUM MUTANE NA MASU ALBARKA_* *_Maza ku matso MASOYAN Bilyn Abdull da IDANU suka hana karatun novels...._* *_Tofa Bilyn ku ta samo muku hanya mai sauƙi da kina aiki, ko kina kwance kina hutawa, ko kina inda baki son yawan surutu earpiece ɗinki kawai zaki maƙala a kunne ko Bluetooth kisha sauraren littafin KIƊA A RUWA.... Cikin sauƙi.... 💃_* *_Kar dai na cika ku da zance. Zamu fara saida littafin KIƊA A RUWA.... Na saurare (Audio) kenan akan farashi mai sauƙi da rahusa._* *_Akwai VVIP AREWAPEN kenan 💃_* *_Akwai VIP Telegram 💃_* *_(Ƴan WhatsApp ku haƙura kawai ƴan ta'addar bati sunfi yawa a cikinku gaskiya tsoron rashin m ɗinku nake 😂🤣)_* *_Telegram Audio 2k ne kacal ba tsada 💃. Sai kusaka ta wannan account ɗin👇_* _(2k)_ *9032345899* *_Moniepoint MFB_* *_BILKISU MUSA IBRAHIM_* *_KATI MTN (2k)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya: 👇_* *_Telegram Number 09032345899_* *_Ƴan NIGER🇳🇪 kuma bazamu barku a baya ba in sha ALLAHU zaku biya (Telegram vip 1,500 CFA) domin littafin KIƊA A RUWA..... na ji Audio-vocal. Sai ki biya tanan👇_*. _(1,500 CFA)_ *_+227 98 94 12 81_* *_My NITA_* *Zaku iya kuma tura katin Airtel na ƙasar NIGER shima 1,500 CFA vip telegram* _Shaidar biya👇_ *_Whatsapp number_* *_+227 98 94 12 81_* *_AREWAPEN (Vvip)_* *_Chapters & Audio_* @BilynAbdull *_Ƴan WhatsApp kuzo muyi shawara idan zaku iya amana ayi harkar nan daku 😂, dan bana son a barku a baya duk da dai bakwa ji, ba raga min zakuyi ba na sani duk da ƙaunar da nake muku 🤣😂._* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_*[01-16, 11:37] +234 703 449 6321: 6 ..........“Ku fara da gaskiyar Ojo. Akwai wani abu da bai dace ba. Kuma akwai hannaye da yawa da suka fi mu ƙarfi har a cikin gida. Sai dai fuska biyun su tasa sun zame mana masu lulluɓin biri”.     Shiru ya cika ɗakin. Wani irin sanyi ya ratsa zuciyar Imran. Cikin kasa haƙuri ya furta, “Idan kuwa har akwai masu fuska biyu zan kasance mai tsoro da shakkar mu'amulantar kowa?”.        “Wannan shine gaskiyar magana, amma a ciki akwai ɗaya tamkar da dubu. General Yusuf Shu'aibu Tafida. Col. Haydar Galadima (Faro), Brigadier General Abraham Yohana, yaranmu Dabo, Yusuf. Amma saura duk ka ajiye kowa. Akwai saƙo a ɗakina na ajiye maka, idan ka haɗa da wannan zai baka abinda nake buƙatar ka fahimta. Dan na tabbatar daga yau bazasu sake barinka ka ganni ba.”      Da ƙyar Imran ya iya furta, “Janar ya shiga SIYASA...”          Cak numfashin Zak-Shadow ya tsaya, hakama bugun zuciyarsa kafin su dawo a tare. “SIYASA?!”. Ya furta yana tsatstsare Imran da idanu.       Kai tsaye Imran ya jinjina masa kai. Sai kawai Dada yayi murmurshi tare da wani ɗan lumshe idanu sannan ya sake buɗesu luuu akan Imran. “Na amince kayi aiki da shi Imran....”      Cikin tsatstsareshi da idanun shima Imran ya ce, “Zak… kana nufin kaci karo da mutanen da kowa yaji tsoron ɗaga su?”.      Wani ƙaramin murmushi mai zafi, mai ɗaci ya bayyana a gefen labban Dada. “Ni ba wanda nake tsoro, Imran. Amma gaskiya… ita ce abin da suka hana ni gani tsawon shekaru uku. Ni kaina kuma na yarda da hasashen General, ta irin hanyar da suke kai, kawai zamu bi mu gano su, mu kuma yaƙe su” ya ɗanyi shiru na sakan biyu. Sai kuma ya cigaba da faɗin, “Yau na baka wannan rubutun. Ka tafi da shi. Kada ka bari kowa ya gani a yanzu har Janar. Dan kai kaɗai nake son kayi waɗan nan binciken”       Idanu kawai Imran ya kafeshi da su ya ma kasa magana. Wato idan Zak.. ɗinsa na wani abu a wasu lokutan yakan ga tamkar mai aljanu ko mai gani har hanji da yara kan faɗa. Kai har ɗan duba ma zai iya kiransa, amma yasan duk ba haka bane, tsabar kaifin basira ne kawai da iya sanin kan duniya da mutanen cikinta da ALLAH ya bashi.     Shi ko Dada ganin kallon da Imran ɗin ke masa, sai kawai ya jingina da kujera a hankali ya lumshe idanunsa. A haka ya ce, “Ban san miya baka mamaki ba ka tsaya kana kallona bayan lokacin ka ƙayyadadde ne. Idan rana ta yi zaka gane me yasa naga mutuwa ta fi wannan shari’ar sauƙi.”     Imran ya kasa magana yanzun ma, a haka har lokaci ya ƙare, masu tsaronsa suka buga ƙofa. Miƙewa kawai Dada yayi zai bar gurin, sai kuma ya tsaya ya kalle shi for the last time yasan kafin a sake ganin juna sai bayan shekaru. Dada ya lumshe ido tare da furta masa a hankali kamar sirrin da baya buƙatar iska ta ɗauka zuwa gaba a tsakanin su.       “Ka zama hasken da nake bukata a waje. Ka cigaba da zama UBA kuma nagartaccen MIJI a cikin GIDA”. Daga haka yay gaba batare da ko waiwayen Imran ba. Shi ko Imran ya kasa motsi sai kai-kawo furucin ƙarshe na Zak-Shadow ɗin ke masa amsa kuwwa a cikin kai, dan magana ce a dunƙule ya bashi kuma mai ƙarfi.....    (((★)))(((★)))(((★)))          ★ 2021..... ★        Duk wanda yasan gidan a shekarun baya takwas da suka shuɗe yanzu idan ya zo ba lallai ya gane ba. Domin kuwa gidan nan da Mammah da yaranta tara mai sassa biyu kacal a yanzu ya zama mai sassa da yawa sakamakon iyalanta da suka ƙara yawa. Kamar yanda Dada ya barma Imran wasiyyar dawo da ginin su Ma'aruff a cikin gida a wacan lokacin hakan ta tabbata, duk da kuwa shima Imran ɗin dole ya bar ragamar a hannun Uncle Nasiru sakamakon prison ɗin daya shiga na shekara uku.      Duk da suna cikin ɗacin yanayi Uncle Nasiru yayi abinda ya dace harda kuɗin aljihunsa. Anyi bikin Ma'aruff da Ja'afar da amarensu Shariffa da Lailah, sai dai bikin baiyi armashi ba sakamon jarabawar da wannan ahali suke ciki a wancan lokaci na rasa jigon gidan da suke ma kallon Uba bawai yaya kawai ba. Amare sun tare a gidan Mammah kowace da ɓangarenta, kuma Alhamdullah dukansu masu tarbiyya ne da suka fito daga gidan tarbiyya. Dan kuwa akwai abubuwa da yawan gaske da suka bambanta su da surukar gidan ta farko Nabeeha. Received at 4:11 PM [01-16, 11:37] +234 703 449 6321: 7 .......Cikin matuƙar bala'i da ihu matar ta ce, “Babbar bala'i kai, wlhy bazan yarda ba, dolene ma yaran nan suje police station dan sai nayi shari'a da su.....”      Da sauri matashin malamin nan ya katseta da faɗin, “A'a ranki ya daɗe kada ai haka. Mudai bari a zauna dasu aji miya haɗasu, duk da nasan Naja'atu da Ruƙayya fitinannun yara ne amma basa faɗa sai da dalili...”          “Oh yanzu na fahimta, to kodai kaine ka sakasu su aikata ma saboda kana nemansu? Dan ba abin mamaki bane idan muka dubi yanda malamai suka koma fasiƙanci da ɗalibansu a makarantu”.       “Innalillahi wa'ina ilaihiraji'un, Hajiya wane irin magana ce wannan? Dan na faɗi abinda yake gaskiya kuma sai ki aibantani da yaran da suke tamkar ƴaƴanki. Amma dai.....”        “Teacher Khalil ya isa haka. Ka fahimta kawai ranta ne ya ɓaci. Yanzu dai ka kira gidan su yaran sannan azo min da su nan yanzu nan”.      Sosai ran wanda aka kira da Teacher Khalil yake a ɓace da zancen matar, sai dai bai sake cewa komai ba ransa na ƙuna ya shiga neman layin wanda yasan Yaya ne gasu Ruƙayya, amma fin kira goma bai shiga ba. Ganin ba samu zaiba principal yace ya sake kiran wata number mana, canja kiran yay zuwa ɗayar number da yake da ita, cikin sa'a kuwa ta shiga. Koda aka ɗaga cikin nutsuwarsa yay bayanin daya dace, a ƙarshe ya sanar da ana buƙatar ganin wani nasu babba daga haka ya ajiye wayar ya fita a office ɗin.... Mintina kaɗan Teacher Khalil ya dawo, sai da ya shigo sosai matasan ƴammata biyu suka bayyana. Ta gaba fara ce tas kuma ƙyaƙyawa, siririya daga ganin fuskata kasan zatai rashin ji. Wadda ke biye da ita ma da zasu iya zama kai ɗaya black beauty ce masha ALLAH, itama dai daga ganin fuskar nan kasan zatai tsiwa. Su duka sanye suke da uniform skirt peach color da farar riga long sleeve shirt, sunyi zanzaro da skirt ɗin, sai ɗan ƙaramin baby hijjaf fari shima da iyakarsa matashin ƙirjinsu da ake kiran kamar su da suna ƙwailoli. Daga ƙasa safa ce doguwa data zo har gwiwar ƙafa saboda skirt ɗin nasu kaɗan ya zartar gwiwar sai takalman sandal baƙaƙe na ƴan makarnta. Ga shi dai uniform ne ana saka shi badan ado ba, amma yayi musu matuƙar ƙyau da zaunawa a madaidaicin jikinsu ɗas kamar ka lashesu. Ga wani ƙamshin turare mai sanyin daɗi na fita a jikin nasu da gogaggun uniform ɗin su da suka sha karin guga kamar batun safe suka sakasu ba.      A makarantar ba'a dukan ɗalibai sam, dan makaranta ce ta kuɗi kuma ta ƴaƴan manyan ƙasa. Duk wanda aka gani a school ɗin lallai ubansa yaci ya ƙoshi ne. Shiyyasa daga ƴaƴan masu mulki saina jami'an gwamnati dana manyan ƴan kasuwa. Dan makarantar ma ta baƙin haure ce ƴan ƙasar waje ba ƴan ƙasa ba. Rabi da kwatar malaman cikinta duk masu jajayen kunne ne, sauran tsiraru irinsu Teacher Khalil ne kawai ƴan ƙasa baƙaƙen fata, sai kuma shi kansa principal ɗin shima dai ɗan ƙasa ne.       Da farko idanu principal ya zuba ƙyawawan ƴammatan biyu, yayinda matar nan ke zuba musu uwar harara kamar idannunta zasu zubo. Hakama ƴarta dake lafe a jikinta tun shigowar yammatan dake sa'ointa ta sake mannema uwarta tana harararsu. Suko sun wani tamke fuskoki suna cika suna batsewa. Haɗa ido baƙar tayi da yarinyar, tako watsa mata uwar harara da nunata da yatsu biyu alamar saita tsokale idon...      Wani irin takaici ya sake mamaye zuciyar uwar, dan ta kasa gane ita zata tsokalewa ido ko ƴar tata tunda itama hararar take. Baki ta buɗe zatai magana principal ya katseta sakamakon ambaton sunan yaran da yayi.        “Ruƙayya Imran Abbas”.   A cinkushe farar tace, “Yes Sir!”. Ya sake maida idonsa ga baƙar ya ce, “Naja'atu Muhammad”. Itama cikin tura baki tace, “Yes Sir”.       “Ku miyasa bakwa jin magana ne, yara kamar ibilis ne malamin ku kullum cikin kawo ƙararku ake. Yanzu ku duba yanda kuka fasa mata kai, inda abin yazo da ƙaddara fa...?” Received at 4:11 PMReactions:[01-16, 11:37] +234 703 449 6321: 8 .......Adeel ibn Ubaidullah Qureshy. Cikakken balarabe ne ɗan asali gaba da baya. Jinin sarauta dan kuwa daula babba suke da ita a yankin larabawa. Sannan zuri'arsu zuri'a ce mai ɗunbin dukiya da kaso huɗu na arziƙin Dubai yana da alaƙa da shi. Adeel irin gagararrun yaran nan ne da giyar mulki data kuɗi ke ɗawainiya da su. Dan kuwa iya shegen da yake zubawa a cikin Dubai ba'a magana.      Harkar business ce ta haɗashi da Hajiya Hasiba, a dalilin First Lady da suke aminta. Sunyi wani zaman meeting Hajiya Hasiba ta kasance kujerarta kusa data Adeel a meeting room ɗin, irin ta ajiye wayarta a table sai aka irin kirata ɗin nan, bata ɗaga ba kasancewar suna a halin meeting har kiran ya tsinke, dai-dai screen ɗin wayar na komawa yanda yake ƙyaƙyƙyawan hoton Nabeeha dake a fuskar wayar Hajiya Hasiba ya bayyana. Sai ko karaf a idon sa. Cak ya tsaya da bayanin da yake ya zubama wayar ido, abokan meeting ɗin nasa sukaji shiru duk sai suka ɗago suna kallonsa, cike da basarwa ya ɗauke idanunsa ya cigaba da jawabinsa, amma bini-bini idonsa nakan screen ɗin wayar Hajiya Hasiba har aka tashi.       Hajiya Hasiba ta lura da kallon da Adeel kema wayarta, amma sai bata kawo komai a ranta ba har suka wuce. Mizai faru da daddare kawai sai ga Firt lady ta kirata wai Adeel nason magana da ita, idan ba damuwa kuma so yake su haɗu. Mamaki ya kama Hajiya Hasiba, ta tambayi ko lafiya? First Lady ta bata amsa da cewar wai akan wani hoto ne da ya gani a fuskar wayarta sanda suke meeting. Sosai Hajiya Hasiba ta zaro idanu tana dafe baki, kafin ta ce, “Kai ranki ya daɗe ɗiyarki ce fa Nabeeha, kin san dai tana da aure kin kuma san waye mijinta da fitinarsa”.      Cikin nuna rashin damuwa First Lady tai murmurshi da faɗin, “Yo ALLAH na tuba sai me Hajiya Hasiba, aure nawa ne a wannan zamanin da shi gara babu. Ke dai kawai ai sha'ani. Mijinta kuwa girman kansa na banza ba ko sisi, kin san waye kuwa Adeel? Hummm na baki dama daga nan zuwa minti talatin ki bincika sai ki yanke hukunci. Ni dai na isar da saƙo yace zai turo mota a ɗaukeki a kaiki inda yake ”. Daga haka ta yanke wayarta.      Shiru Hajiya Hasiba tai na tsawon lokaci, dan babu abinda ke zuwa mata a zuciya da brain sai fuskar Zak-Shadow. Amma dai ta daure ta fara binciken waye Adeel kamar yanda First Lady ta bata shawara. Tun a ambaton farko kanta ya nema bugawa, jin nasabar gidansu kawai, jin ɗan waye daga zuri'ar daya fito. Data bincika arziƙin zuri'ar tashi kawai bama shi wadda ya mallaka ba bata san ta rikito a kujera ba tsabar rawar jiki. Har lokacin da za'a ɗauketa yayi bata iya ta dawo a hayyacinta ba saboda matsanancin mamaki. Ai babu ɓata lokaci ta shirya a gurguje tabi ɗan aiken. Ai ko kanta da zuciyarta sun nema fashewa saboda inda aka kaita matsayin wajen hutawarsa. Wani mahaukacin azababben garden ne da in ka kirashi da suna aljannar duniya bakai ƙarya ba. Ga masu hidima zagaye da wajen da wasu mugayen masu tsaro ya subahanallah. Ita dai haka aka kaita har inda yake jiki na ɓari.      Kallo ɗaya yay mata ya maida kansa ga laptop ɗin gabansa, a haka cike da isa ya nuna mata wajen zama. Sai ta dinga jin kamar ba Adeel ɗin juya bane da sukai zaman meeting, koda yake ko'a jiyan dama yanda yake magana da isa da ƙasaita kasan akwai girma da izza. Amma a yau ɗin ba'a magana. Ya share fin mintuna goma sannan ya gyara zamansa, babu wani tauna harshe ko girmamawa kai tsaye yana kallonta ya furta, “Yarinyar dana gani kan wayarki nake buƙata, ina fatan ba hotonki bane dan naga kuna kama sosai, tsufa kawai zaki nuna mata”.      Kan Hajiya Hasiba a ƙasa tana murmurshi ta ce, “A'a bani bace. First born ɗina ce, sunanta Nabeeha”.       “Nice...”    Ya faɗa cike da iskanci yana ajiye kofin hannunsa. Sai da ya ƙara busar iska ya cigaba da faɗin, “Za'a iya kawo min ita a yau? Zan bada ko nawa ake buƙata, daga biliyan 1 zuwa sama”. Received at 2:42 PMReactions: [01-16, 11:37] +234 703 449 6321: 9 ..........“Sir kawai fa dan na taka ita Ruƙayya ɗin ne ban kula ba, kafin na bata haƙuri sai ta hankaɗe ni ta ƙwace wayata ta jefar a ƙasa ta fashe, ni kuma na zuba mata ruwa a jiki ƴan class suka yi dariya. Itafa Nimrah ɗin ma bata ajin ta fita, kawai tana shigowa ba tambayar ba'asi ta hau dukana itama Ruƙayyan na tayata, ni kuma naji wahala na cijesu kawai suka gwara kaina da bango wai aljanunsu ya tashi...”         “Da dai kin fito kin faɗi gaskiya yarinya da yafi miki”. Cewar Ruƙayya tana hararta. Uwarta zatai magana principal yay saurin tarar numfashinta. Idanunsa akan su Ruƙayyan ya ce, “Ke haka akai?”.       “Sir ta ɓoye asalin zancen”.    “To miya faru?”. “Yarinyar nan ƴar iska ce Sir, a bayan desk ɗinmu suke ita da ƴar iskar ƙawarta, kullum sai suna damunmu da kallon Film ɗin iskanci a waya, mun musu magana akan idan suna kallon rashin tarbiyyarsu a waya suna saka Bluetooth amma sun ƙi dainawa. Kawai yau suna kunnawa na juya na ƙwace wayar na fasa banza, shine tazo zata min hauka ni da Ninah muka sauke mata nata ƙaramin hau ɗin”.      Rawa jikin yarinyar ya fara, ta fara rantsuwa ita sharri su Ruky sukai mata. Uwarta ma bala'i ta fara wai za'a ma ƴarta sharri bazata yarda ba. Kodai principal ya bari ƴan sanda su tafi dasu Nimrah ɗin ko kuwa tai ƙarar makarantar gaba ɗaya. Cikin takaici Ammar ya ce, “Hajjaju ya kike Abu kamar baƙya ganewa ne, shin anan akwai wai mai tsoron zuwa police station ɗin ne anan akace miki. Yaran nan sun faɗi abinda ya faru har sukai rikici da ƴarki, maimakon ma ki damu da abinda take aikatawa kina neman juye wa mutane shirme. To muma bazamu yarda ba, dan bazata ɓata mana tarbiyyar yara ba, banda ma rashin kula har yara na kallon banza da wofi a waya iyaye basu sani ba, kuma miye na zuwa da waya makaranta? Gasu nan ko waya basu da ita yaran nan kuma basu taɓa damuwa ba duk da sun kai ƴammatan daya dace ace an barsu da ita, idan anyi maganar ku daina bama yara waya ko ku dinga kula dasu idan kun basu musamman masu tashen sabuwar balaga irin su kuga kamar an raina ƙoƙarinku ne. Ba haka bane, a irin wannan gaɓar waɗan nan abubuwa suke kwaɗaituwa a zukatansu, dan haka muma bazamu yarda ba, yaranmu masu tarbiyya ne, bakuma za'a ɓata mana su anan ba, kuma yanda sukai mata sun min dai-dai....”     Hayaniya sosai ta kaure a office ɗin tsakanin Hajiya da Ammar, sai da ƙyar aka fitar da Ammar itama Hajiyar principal yace taje zasuyi bincike akai. Dan haka an bama yaran suspension na sati ɗaya su duka ukun har sai an tabbatar da gaskiyar mai laifi. Suko ƴan sandan data kira suka sallamesu. Suma ƴan sandan sanin makarantar ta jiga-jigai ce basu ja da nisa ba suka wuce.        Yaya Ma'aruff dake hararar su Nimrah ya ce, “Sai ku wuce muje masu kunnen ƙashi. Hankalinku ya kwanta ai ko. Banda ma fitina ku kuma haifeta da zaku hukuntata? Ba kusan hanyar kai report bane, jibeku da kawuna kamar kullun magani”.      Babu wanda a cikinsu bai cika baki da iska ba. A haka suka fito suka shiga mota shima Yaya Ammar na zuba musu tashi hararar.....           ★ Koda suka iso gida ko kallon inda suke su Yaya Ma'aruff basuyi ba suka shige ciki abinsu. Kallon juna Nimrah da Ruƙayya sukayi, cikin marairaicewa Ruky ta ce, “Wlhy yau akwai matsala Trouble Queen....”     “Babba ma kuwa”. Aka faɗa daga bayansu, a tare duk suka juya, Mu'azz ne daya zama matashin saurayi ɗan shekara goma sha takwas, dan kuwa ya kammala Secondary ɗinsa ma yana shirin shiga jami'a. Yanzu kam Nimrah ce tace, “Ya Mu'azz kaji tsoron ALLAH”.          “Oh, to da tsoron ku nake ji. Ba kunce ku baƙwa jin magana ba. To Daddy ma na nan zuwa dan Uncle J ya kirashi shima”. Wani mugun ƙwalalo idanu waje sukayi a tare, shi ko ya kwashe da dariya yana barin wajen. Da sauri sukabi bayansa, amma yaƙi tsayawa har suka shigo falon. Cak kuwa suka tsaya, ganin kowa yana nan har su Aunty Lailah. Yaya Ja'afar ne ya fara zuba musu harara da faɗin, “Sannunku ƴan wrestling ko ƴan boxing ma zance ban sani ba nikam”. Received at 2:42 PMReactions:[01-16, 11:37] +234 703 449 6321: 11 .........Kwanaki kusan biyar su Nimrah na cin ƙaniyarsu da aiki, sun jikatu matuƙa sunyi laushi, kuka da roƙo babu kalar da basuyi ba, hakama kawunansu sun bama Daddy Imran haƙuri amma yace idan suka bar aikin nan Boarding fa babu fashi. Da ga ƙarshe dai suka zagaye suka kira Aunty Ummie a waya suna mata kuka suka sanar mata. Dama kwana biyu bata leƙo gidan ba saboda aiki. Aunty Mommy kuwa basa ƙasar ita da mijinta sai a satin nan zasu dawo. Ita ko Aunty Mimi ciki gareta tsoho haihuwa ko yau ko gobe shiyyasa Mammah ta hanata zuwa gidan.      Alhamdullahi zuwan Aunty Ummi da suke kira da Big Mah-mah ne ya cecesu a hannun Daddy Imran. Dan bayan an sako massalacin juma'a yazo gidan gaida Mammah ta tareshi da daɗin baki da ban haƙuri har ya haƙura masu aiki su dawo gobe. Amma duk da haka da sharaɗin daga yanzu kullum dasu za'a dinga shiga kitchen yin girki. Da wannan ALLAH ya ƙwacesu. Masu aiki suka dawo, su kuma suka samu sauƙi. A cikin satin ma suka koma zuwa islamiyya dan suspension ɗin ta ya ƙare, sai kuma karatun da akayi basa nan ya sakasu a gaba. Sati ya zagayo suka koma boko ma, amma duk da haka sai da akai zama da Hajiya ta kafa sharaɗin babu su ba yarinyar ta, dole kuma a raba musu wajen zama sannan case ɗin ya mutu. Dan an dai gane ƴarta na kalle-kallen banza a waya da gaske kamar yanda su Nimrah ɗin suka faɗa......         >>>>><<<<<<     Yau ta kasance juma'a, dan haka an tashesu da wuri. Sai dai shiru babu drivern su babu alamarsa. Sun san maybe ya fara zuwa ɗaukar su Abees kafin yazo nan, duk da kuwa a kulum su yake fara zuwa ya ɗauka kafin su ƙarasa makarantar su Abees ɗin saboda suna rigansu tashi. Tun suna kallon agogo har suka sare, ga mafi yawan ɗalibai duk sun wuce anzo an ɗaukesu. Makarantar su nada doka kuma ma tilas zuwa ake ɗaukar kowane ɗalibi bawai buɗe musu gate ake su fito ba kawai.      Sun gaji ga Ruky na ciwon mara, dan ita in zatai period ba ƙaramin jikata take ba. Ganin ta fara kuka hankalin Nimrah ya tashi. Ofishin Principal ta nufa amma ta tasar baya nan wai sun shiga meeting da malamai. Da gudu ta dawo wajen Ruky, ta sameta durƙushe azaba ta isheta, bata son suje clinic ɗin cikin makaranta dan an riga an tashi. Idannunta na cika da ƙwalla itama ta kamata ta miƙar. “Tashi muje wajen security ko zai taimaka ya barmu mu fita kawai, amma shima Baba Driver bai ƙyauta mana ba”. Da ƙyar da ƙyar Ruky ta iya miƙewa suka isa gate ɗin, cikin sa'a suna isowa sai ga motar Yaya Ammar na isowa. Ajiyar zuciya Nimrah ta sauke, dai-dai Mu'azz na fitowa daga motar, ya ƙaraso inda suke da sassarfa yana faɗin, “Lafiya kuwa? Miya sami Ruƙayyan?”.         “Yaya ciwon mara, muyi sauri mu tafi kasan idan ya fara tsanani sai suma. Amma Yaya driver fa?”.       Sai da ya buɗe musu suka shiga yake bata amsa yana reverse. “Baba driver accident yayi, yanzu haka ma yana asibiti”.      “Innalillahi wa-inna ilaihiraji'un, badai da su Aheel ba?”.      “A'a bada su ba, shi kaɗai ne yaje ɗakko motar Ummie (Aunty Lailah suke cema Ummie, Shariffa Ammie) daga wajen wanki”.         “Ya rabbi, ya jikin nasa?”.     “Gaskiya yaji jiki sosai, dan har yanzu ma ba'a bari an gashi ba. Motar kuwa tama tashi aiki, dan babbar mota ce ta haye shi”.       Gaba ɗaya jikin Nimrah ya ƙara sanyi, ita kanta Ruky dake fama da kanta hankalinta ya sake tashi, a haka suka iso gida ciwon marar ya ƙara tsanani, dole ma sai Mu'azz ɗaukarta yayi. Gaba ɗaya hankalin ƴan gidan a tashe yake da hanlin da baba driver ke a ciki, dan mazan gidan duk suna can. Ganin hanlin da Ruky ke ciki kuma duk sai suka maida hankali a kanta. Babu bata lokaci aka kira family doctor ɗin su, da yake ya san matsalarta yana zuwa allurai yay mata....      Basu sami ganin Baba Driver ba sai ranar Lahadi da yamma. Gaba ɗaya gidan suka shirya suka je suka duba shi. Yaji jiki kam kwari da gaske, amma Alhamdullah yana samun dukkan kulawar data dace. Ga matarsa an ɗakko tana jiyyarsa. Komai na asibitin Kuma su Yaya Ja'afar ne suka biya. Received at 6:57 PM [01-16, 11:37] +234 703 449 6321: Sannan ya kamata mu yarda ba laifinsu bane akan abinda ya faru baya, shima kansa wanda ake son azabtar da su ta dalilinsa mufa sani rayukanmu ya jajirce wajen karewa, ALLAH ne ya ƙaddara za'a tarwatsa mu a ƙauyukanmu har mu watse irin haka. Hasalima mutanen nan dake munana shi a garemu sune silar faruwar komai akan waɗan can abubuw......”         “Rabe! Kana nufin wuyanka yayi kaurin bijirema su Oga Dagger ko? Amma kasan minene hukuncin yin hakan a gareka ko? Karka manta kana cikin ƴantattun da aka bama damar zuwa su rayu a cikin mutane har suyi aure su hayyafa cikin ƴanci. Baku san wahala da azabar da mu dake cikin jeji kullum a ɓoye muke sha ba. Mutanen nan da kake ƙoƙarin karewa ance maka kaje kai musu wani abu ne? Information ɗin abinda ke gudana a rayuwarsu kawai akace ka dinga kawowa. Musamman ita wannan yarinyar Nimrah, amma taurin kai yasa ka zauna kana kawowa mutane ƙauli da ba'adi, gashi nan har sai da ka jama kanka zaman guri ɗaya, da da ƙarar kwana ma yanzu wani labarin ake ba naka ba. Ni dai yanzu ga saƙo, Oga Mole da Oga Dagger sunce gobe zasu turo sabon driver ka turashi ga mutanen nan ya maye gurbin ka, zaɓi ya rage naka kayi koka kuskure kai ne zakai kuka, dan a yanzu ba kai za'a hara ba ƴaƴanka ne ko matarka”...       Yana gama faɗa ya miƙa batare da ya saurari magiya da roƙon Baba Driver ba..... ★>><<<<★>>>><<★         ★DUBAI★    Ganin yanda Nabeeha ke faman haɗa kaya ya bama Ismat data kawo mata breakfast har ɗaki tsoro. Duk yanda taso daurewa saita kasa. Cikin damuwa ta ajiye tray ɗin da take ɗauke da shi ta nufeta. Hannunta ta riƙe cikin rauni da damuwa ta ce, “Aunty wai mi kike yi haka ne? Ina zaki kike haɗa kaya?”.          Hannun nata ta fisge, kukan da take faman riƙewa tun daren jiya saboda taurin zuciya a karo na farko ta fashe da shi..........✍️ Received[01-16, 11:37] +234 703 449 6321: 12 .........“Ismat zan koma ƙasata, wlhy na gaji da wannan rayuwar, bazan iya ɗaukar huɗubar Momy ba, gara na koma gidan mijina nai zaman jiran dawowarsa ko nan da shekara hamsin ne ma ba ashirin da biyar ba”.        Ajiyar zuciya mai ƙarfi Ismat ta sauke, dan koba komai itama an taɓo mata inda ke mata ƙaiƙayi dama. Ta kama hannun Nabeeha suka koma bakin makeken gadon ɗakin da yaji shinfiɗu na alfarma, dan duk da haɗuwar gidan da komai na cikinsa ɗakinta na musamman ne. Gyara irin na ƴar gata Adeel yasa akai mata. Hannayenta duka a cikin na Ismat ta ce, “Aunty wlhy koni ina bayanki ki koma gidanki, dan ita Momy idannunta sun rufe da son kuɗi bata duba abinda muke so koya dace damu. Ita kawai tafi kallon abinda zata samu. Gamu dai a cikin ƙaton gida a kuma ƙasa irin ta Dubai da kowa ke buƙatar yazo, amma wlhy Aunty Jiddah ta fimu kwanciyar hankali, tana rayuwar auren ta ga yaranta abin sha'awa, shiyyasa wlhy nima na fara ji a raina zanyi na nata na koma gidan Abba na bashi haƙuri na samu miji nayi aure. Dan in har muka cigaba da rayuwa da Momy anan wataran sai mun lalace, dan waɗan nan shaggun mutanen babu abinda suka iya sai son mata kamar su babu matan a cikin nasu ƙabilar”.        “Ismat wlhy ni duk bama wannan ba, babban abinda ke bani mamaki da Momy itafa kawai na kashe aurena saboda wannan mutum yace mata aurena yake son yi, haba miyasa ba zatai tunanin daya dace ba, dukiya irin ta mutumin nan, da nasaba ta gidan mulki, mulkin ma mai ƙarfin gaske ne zai zauna wani auren baƙar fata ƴar Africa saboda rainin hankali da ɗaukar mutane jakai. Kiga yanda suke wulaƙanta matan African fa kamar wasu dabbobi dan ko bayi na baya sun fi matan da ake kawo musu suna iskanci da su a yanzu mutunci da daraja. Wlhy Ismat ina son mijina, duk da ina jin takaicin auren shegiyar yarinyar nan har yanzu a zuciyata....”        “Na sani Aunty, ki share wani batun yarinya kawai muyi tafiyar mu, dan uwarta mune zamu miki maganinta, da ƙafarta zata bar gidan batare da kowa ma ya sani ba ta koma ƙauyen su, idan tace ita ƴar hau ce mu ƴan hau-hau ne to”.      Ajiyar zuciya mai ƙarfin gaske Nabeeha ta saki, tana mai jin nutsuwa da gamsuwa da zancen autar tasu. A gefe zuciyarta na jin matsanancin kewar mijinta da buƙatar son kasancewa da shi da akoda yaushe take yaƙi da kanta a kai, sauƙi-sauƙin ma da take samu kullum cikin mafarkinsa da yanda yake tafiyar da ita a shimfiɗa take, shiyyasa take samun sassauci da jinsa kamar a kusa da ita har yanzu.....         Da baya-baya Hajiya Hasiba tabar bakin ƙofar ranta a matuƙar ɓace da tattaunawar yaran nata. Ƙayataccen ɗakinta ta shiga, ta zauna a bakin makeken nata gadon hannunta dafe da kanta. Jitake kan nata na wani mugun sara mata, sai dai abinda ke mata kai-kawo na takaicin yaran nata na son danne ciwon. Lallai lokaci yayi da zata nunama su Nabeeha ita ba sankaran uwa bace sha-sha-sha kamar yanda suke tunani. Taya zata bari ma Nasiru yaci nasara a kanta, bayan ya rabata da Jiddah ya rabata da Nabeeha da Ismat da suka rage mata kuma. Ta jima da fahimtar soyayyar da Ismat kema Ja'afar, sai dai bata damu ba ganin yanda shi Ja'afar ɗin yaƙi kulawa, amma yanzu ta fahimci Ismat na zuga Nabeeha ne su koma gidan ubansu saboda son da take ma Ja'afar, kenan da sunje sun kwantar ma da ubansu kai itama sai ya aura mata shi, shekenan ita kuma A'isha ta haifama ƴaƴa ko? To kuwa zasuci ubansu.       Da wannan tunanin tai ƙwafa, tare da miƙewa zuwa gaban wadrobe ɗinta, ta ɗibo duk passport ɗinsu dake wurinta, cire na Nabeeha da Ismat tayi ta canja musu waje, daga haka ta hau shirin fita. Dan tana buƙatar ganawa da Adeel yanzu nan basai gobe ba.....         §§§§§§§§§§§§§§§§        ★EGYPT ★                     “Mammah muje ki huta yau kam kin gaji fiye da kullum. Ga su Yaya Ma'aruff nata kira nasan burunsu kawai suji yanda results ɗin suke ne. Aunty Ummi ma naga ta kira video call ta WhatsApp”. Received [01-16, 11:37] +234 703 449 6321:       Murmushi Mammah tayi, cikin sauke ajiyar zuciya ta ce, “Ammar yarana duk sunyi kewata ne, nima ina tsananin jin kewarsu. Dan haka ni kam ba sai sati biyun nan ya cika ba zuwa jibi tunda sunce babu wata damuwa suna bamu maganin nan kawai mu koma gida”.          “Duk yanda kike so haka za'ai Mammah”. Yay maganar yana ɗan rungumota ta gefe, dama kuma suna tafiyar ne hannunta riƙe a nashi. A yanda ya ɗan rungumetan yana dariya itama yana murmurshi da kai masa rankwashi a kai yasa basa kallon gabansu balle mai tahowa. Karaf kuwa sukaci karo da wani abun da ya saka Mammah faɗin, “Subahanallahi”. Shima sai Ammar ɗin ya sake ta yana waiwayawa da ambaton, “Ya salam”. A dai-dai lokacin shima wanda sukai karon ya ambaci, “Subahanallahi” ɗin yana kaiwa duƙe da son riƙo takardun hannunsa da suka tarwatse a ƙasa. Cikin sauri Ammar ya bishi shima yana ƙoƙarin taimaka masa da sake faɗin, “I'm sorry sir”.        Fuskar mutum da murmurshi ya ce, “Karka damu ɗana, nima harda nawa laifin hankalina nakan takardun ne shiyysa ban lura da tahowarku ba. Mama kiyi haƙuri kem......”     Ya kasa ƙarasawa saboda dai-dai ya ɗago ne zai kalla inda Mammah ɗin take sukai ido biyu. Dan itama ta miƙo masa takardar data ɗakko ne datai gefe zatai magana a lokacin, sai ta dakata cak tana kallonsa. Ko shekara dubu tayi bazata manta wannan fuskar ba a duniyarta, balle shekarun da basu wuce talatin ba. Jin sunyi shiru Ammar daya gama tattarowa shima ya juyo yana kallon su, Mammah ya fara kallo datai tsaye ƙyam baki buɗe tana kallon mutum, da sauri ya maida kallonsa kansa shima. Ai da sauri ya wani ja baya yana waro idanu waje da faɗin, “Ya rabbi! Mammah waye shi?”.       Mammah da gaba ɗaya kanta yay wani dimmm ta gagara cewa komai, sai hannunta dake ƴar rawa har sai da Ammar ya matso ya riƙota jikinsa, sai dai har lokacin idanun nasa akan mutumin da alamu ya nuna shima dai yayi sumar tsugunne ne......         >>✿<<>>✿<<>>✿<<                    “Assalamu alaikum”.     Aka kwaɗa sallama daga bakin ƙofar falon bayan anyi knocking har sau biyu. Ƙaramin tsaki Mu'azz dake zaune shi kaɗai a falon yana cin abinci yaja, ya tsani tashi yana cin abinci, dan yana tashin shike nan abincin ya fita a kansa kuma. Hanyar kitchen ya kalla inda yake jiyo surutun Nimrah da dariyar Biebah. Sai kawai ya ɗaga murya ya ce, “Ninah!”.        Daga can ta ce, “Kai Yaya Mu'azz miye kuma dan ALLAH? Bana kawo maka harda ruwa ba”.           “To uwar son jiki, dalla fito kiga waye ana knocking ne”.       Baki a sama ta fito, tana sanye cikin shirt da riga na lass milk da furanni coffee. Tayi ƙyau sosai daka ganta kaga ƴammatan zamani masu shegen iyayi da rawar kai. Harta nufi ƙofa ya ce, “Haka zaki fita ba hijjab?”. Baki ta ƙara turawa gaba, ta dawo ta ɗauka hijjab da sukan ajiye a falon saboda irin haka, dan Mammah ta saba musu sakawa musamman idan akai baƙon ido ko suka saka ƙananun kaya, wani lokacin ma sai taga kamar anfi takura mata da sakawa fiye da Ruky da Aunty Biebah. Sai da ta saka ta zura hannayensa sannan ta nufi ƙofar da aka sake bugawar, sallamar maigadi ta amsa tana buɗe ƙofar. Ya ɗan ja baya yana gaisheta.           “Baba ni dai ka daina rissina min dan ALLAH. Ina wuni?”.     Murmurshi maigadin yayi da faɗin, “Ai girmanki ne Hajiya. Dama baƙone yazo yace kuma sabon driver ne Malam Buba tsohon Driver ya aikosa”.      Ɗan jimm tayi sai kuma ta ce, “Okay to bari na sanarma Yaya Mu'azz, dan su Uncle's duk basa nan. Ammie da Ummie ma sun tafi gidan Mom (Aunty Mimi suke kira Mom) data haihu ɗazun”.        Fuska ɗauke da murmushi ya ce, “ALLAH sarki ALLAH ya raya, ya albarkaci abinda aka samu”.      “Amin ya rabbi”. Ta faɗa tana rufe ƙofar ta juya ciki. “Yaya wai sabon driver ne, kuma Baba Driver ya turoshi”.      Ɗagowa Mu'azz yay yana kallonta, sai kuma ya maida kansa ga television yana faɗin, “Oh to sannunsa da zuwa. ALLAH ya iyakance min jigilarku kullum kuna damuna da surutun ku da fitina. Ki haɗa abinci ki kai masa dan abinci nake ci sai na kammala na fita mu gaisa”. Received[01-16, 11:37] +234 703 449 6321:           Sai da ta cika baki da iska cikin ƙunƙuni ta nufi kitchen tana faɗin, “Ni wlhy yau ƙafafuna duk ciwo suke, dan anga Mammah bata nan sai wahala ake bani, yau tunda muka dawo school ban huta ba komai ni....”      Fiiiffgg! Filon kukera da Mu'azz ya jiho ya sameta a baya. Tako dage ta ƙwalla ƙarar data saka Biebah fitowa daga kitchen da gudu tana tambayar lafiya da riƙo Nimrah ɗin. Kai Mu'azz ya girgiza cike da takaici yana nuna fillon daya jefeta da shi.        “Small Mom fillo fa kawai na jefa mata dan tana min ƙunƙuni shine take wannan ihun. Wlhy Ninah kiji tsoron ALLAH. Wai uwar wa ma ya hanaki bin su Ammie ne kamar yanda Ruƙayya tayi?”.         “ALLAH sai na gayaka da Uncle, kuma ai dai naji zafi. Tunda na dawo kaketa sani aiki, na maka gyaran ɗaki, kace na maka ɗan wake, duk baka gani ba sai da ka ci zalina”.      “Oh gori kike min saboda kin min gyaran ɗaki da ɗan wake? Lallai ma Ninah ni ko”.     Kai Biebah ta girgiza da jan ƙaramin tsaki ta koma ciki tana faɗin, “Kudai bazaku taɓa canjawa ba ALLAH ya shirye ku. Ba sai ku cinye kanku ba jarababbu. Wlhy na ƙagara Mammah ta dawo gidan dan kun isheni”..........✍️      [01-16, 11:37] +234 703 449 6321: 15 ........Shi ma'abocin ibada ne da ƙoƙarin ganin ya kiyaye dokokin UBANGIJI da kusantuwa da shi a lokacin da yake rayuwa kamar kowa. A yanzu daya ɓuya bisa faifan ƙaddararsa da jarabawa da makircin masu makirci hakan bai sauya komai ba. Sai himma da dagiya da hakan ya ƙara masa wajen sake kaɗaice UBANGIJI da bauta. Halin da yake ciki bai taɓa sakawa yaji kasawace ko tauyewa daga UBANGIJIN SA ba. Bai kuma taɓa jin nasara ce ga azzalumai ba. Bai taɓa mantawa da ƙasar da talakawan ƙasar ba. Yanda yakema kansa addu'a da zuri'arsa haka yake addu'a ga ƙasa baki ɗaya.      Tabbas a siffa ta jikin ƙarfi da ALLAH ya bashi zuwa yanzu ya risina, sakamakon canjawar tsarin abincinsa zuwa zaɓin wanda ake ciyar da shi a yanzu. Shiyyasa ya zaɓi ɗaukar matakin yin azumi yau, gobe ya huta, azumi ibada ce mai girma, sannan kariya ce daga jarabawar ɗan adamtaka ta lafiya da halittun jiki da UBANGIJI ya ni'imata mu da su musamman akan abokan rayuwa. Nauyin jiki da raunanuwar ƙarfi bai sa ya gaza wajen ƙoƙarin cigaba da ƙarfafa ƙashi da tsoka da sauran ƙarfin daya rage masa ba, dan a cikin wannan nan dai tsukun ɗakin da yake ciki yakan gudanar da ibadarsa ya kuma motsa jiki da salo-salo irin nashi. Rashin ƙarfafa damuwa a zuciya, ya bashi kariya daga cututtukan zamani irin su hawan jini balle ciwon zuciyar da maƙiya ke fatar masa a kowane motsinsu. Ya riga ya amince UBANGIJI shine mai komai da kowa, idan kunga alkairi daga gareshi ne, saɓanin hakan daga shaiɗan ne ko halayenku ko jarabawar da zata sake ɗaukaka darajar ku zuwa wani mataki na duniya ko lahira. Yayi imani da hakan shiyyasa damuwa ta kasance abu na ƙarshe da zai iya cewa yana yi. A duk sanda ya tuna da ahalinsa musamman jajirtacciyar uwa irin Mammah, yakan mata addu'a da fatan samun nutsuwar zuciya daga shiga damuwar halin da yake a ciki. Hakama ƴan uwansa da suke masa kallon uban da matarsa daya tabbatar soyayyarsa mai ƙarfi ce a zuciyarta. Hatta ƴar amanarsa tana nan zaune daram a zuciyarsa, yana kuma mata addu'a da fatan rayuwa mai nasarori a yau da gobenta, sai dai daga ita har Nabeeha yana jiran wani lokaci ne da zai sawwaƙe musu suje suma su sake gina sabuwar rayuwar su.        Bai yanke hukuncin fita a wannan wajen ba, dan bashi da wani tabbacin fitar. Sai dai yana fatan aikin daya ɓuya domin yinsa da hana Imran shiga cikin tarnaƙin su tabbata. Dan in har ALLAH ya bashi tsohon rayuwa a kurkukun nan, akwai matsayin da Imran zai kai a gidan soji da zai sa babu wanda ya isa hanashi zuwa ziyartarsa a-kai-a-kai. Idan kuma har UBANGIJI ya bashi damar cika shekarun da suka ɗiba masan ya tabbatar lokacin da zai fita koda bashi da ƙarfin jiki dana aiki, yana da zuciyar bin waɗan can azzaluman ɗaya bayan ɗaya ya hukunta su da hannunsa. Balle ma ko a yanzu ya gama shirya in har yay wasu shekaru a wajen nan sai ya nema hanyar dinga fita yana aiki yana dawowa koda a ƙarshe zai bayyana kansa a ƙarasa yanke masa hukuncin ɗaurin rai da rai koma kashe shi kai tsaye....        Motsin buɗe ƙofar da akai ya saka tunaninsa katsewa, dan yana duk wannan tunanin ne tare da push-up daya sabama kansa yi sama da ɗaruruwa a kowane rana koda yana azumi. Dan haka har yanzu jikinsa a bubbuɗe yake sai dai raguwar ginanniyar tsoka da bata samun sinadarin da take buƙata kamar baya. Daga yanda yake push-up ɗin kawai ya ɗan ɗago idanunsa ya kalla yaran sojin guda biyu ya janye yana cigaba da abinsa.      Suma sake nutsuwa duk sukayi, dan su sun san badan zaki na keji ba basu isa ziyartar ko gefen dajin da yake farauta ba. A tare suka ƙame tare da yin salute ɗinsa, kafin na gefen damarsa ya furta, “Sir kana da vistor ne”.       Cak ya ɗan tsaya na sakan, sai kuma ya cigaba da abinda yake batare da yace da su komai ba. Fin mintuna uku, dan har sai da ya cika adadin da yake buƙata kafin ya tashi da ƙyau tamkar ba shi ya gama push-up ɗin ba yaja ƙaramin towel dake jikin ƙarfen gadon kusa da sallaya ya fara goge hannunsa zuwa wuyansa. Sanye yake cikin uniform ɗin prison ɗin, amma hakan bai hana su kasancewa fes ba alamar baya barinsu da datti, sai dai sun koɗe sosai alamar tsufa da gajiya. Receive[01-16, 11:37] +234 703 449 6321: A karo na farko ya furta, “Tsawon shekaru biyar kenan a tsarin jadawalin da doka ta sharɗanta a kaina No visitors, no communication. Miya canja hakan a yau daga dokar?”.      Sake duƙar da kawuna sukai, kafin ɗayan yay magana cike da girmamawa. “Sir muma bamu sani ba. Umarni kawai aka bamu na zuwa da shi inda kake”.       Idanu ya zuba musu sosai su duka biyun. Wani ɗan murmurshin gefen baki da shi kaɗai yasan yayi kayansa yayi. Ya ajiye towel ɗin a kan ƙarfen gadon ya taka a nutsensa cike kuma da tafiyar nan tasa ta nutsuwa, dattako zuwa gabansu bayan ya saka slippers a ƙafarsa.        “Ku aikata aikin soja, Captains. Na fahimta.”      A tare suka sara masa, zukatansu na sake jin rauni, ƙaunarsa da girmamawa.     “Sir… I’m sorry.” Suka sake faɗa a tare. Bai ce da su komai ba face miƙa musu hannayesa duk biyu. Dan doka ce fita da shi sai da handcuffs. Jikin sojan har ɗan rawa-rawa yake a ƙoƙarin ɗaura masa handcuffs ɗin, haka dai ya gama suka koma gefe suka bashi hanya. Shine ya fara fita sannan suka bi bayansa har ɗakin ganawar. Vistor ɗin nasa ya juya baya, dan haka bai fahimci ko wanene ba sai da ya zauna a kujerar da aka tanada domin shi.....   <<<>>><<<>>>    ★EGYPT★        “Mammah dan ALLAH ki daina kukan nan ya isa haka”.     Ammar ya faɗa cikin tashin hankali muryarsa na rawa idanunsa shima cike da hawaye. Sai kuma ya dubi mutumin da shima ke sharar hawaye ya ce, “Bawan ALLAH ka min bayani dan ALLAH. Minene alaƙarka da Mammah ta? Ku taimaka ku sanar min kada zuciyata ta fashe, dan kukan Mammah ba ƙaramin azabtarwa bace mai ƙuna a zuciyata”.         Hawaye mutumin ya sake sharewa da handkachiff harda ɗan fyatar majina. Kafin ya kalla Ammar cikin rawar muryar alamun tahowar wani sabon kukan ya ce, “Ɗana ka kwantar da hankalinka, duk da ban san wanne a cikin ƴaƴan nawa ba ina ji a raina ko Bilalu ko Abdul-rasheed (Ammar) ne kai. Dan kune dai ƙananu da zan iya gani a wannan shekarun ba Haysam ko su Ja'afar da Ma'aruff ba”.     Kafin Ammar yay magana cikin zafi Mammah ta ce, “Har kana iya cigaba da riƙe zuri'ata a cikin ƙwaƙwalwarka amma ka gagara waiwayen inda nake Tasi'u....?”         “Wlhy Adda A'isha kunya ce ta hanani, tsananin kunyarki nake ji da tsoro da nadamar son zuciyata. Ina ganin bazaki sake kallo na ba a rayuwarki, bazaki sake son ji koda daga wani ne kina da ɗan uwa irina ba. Adda A'isha ni azzalumi ne butulu da ban cancanci gafara daga gareki ba balle marigayi Yaya Abdul-rasheed, dan kuwa mun kasance butulu da ga ni har Bashir da danginsa......”         “Bashir bai kasance butulu a gareni ba, dan kuwa na tabbatar idan shine a raye komai girman laifin da yake ganin ya min bazai ɓoyema ganina a tsaho waɗan nan shekarun ba. Haba Tasi'u, kun maida ni mara kowa a duniya, mara gata, mara dangi gaba ɗaya. Badan Yaya Nasiru ba da nace ban san daɗin zuri'a ba a duniya. Da ƴaƴan Kawu kamar sun waiwayemu munata zumunci har bikin su Haysam duk dasu a kayi suma yanzu sun sake ɗauke min wuta gaba ɗaya saboda ƙaddarar rayuwa da muka sake shiga. Shike nan kowa ya juya bayansa a garemu dangina dana Abdul-rasheed idan ka cire Jamilu da su Khadijah saboda kawai sune ciki ɗaya da Abdul-rasheed. Wlhy idan kowa zai barni banyi tunanin harda kai ba da muke ciki ɗaya Tasi'u, kada ka manta nice na fita a cikin Inna ka kwanta, sannan nice na gama sha daga jikinta ka amsa. Miyasa zaka gujeni tsawon shekaru ashirin da shida, a talatin kaɗan ne babu rabona da kai fa Tasi'u. Miyasa? Miyasa haka?”.         “Wlhy kunya ce kamar yanda na sanar miki Adda, dan ALLAH ki yafeni ki gafarce ni na tuba”.     Yay maganar yana sauka ƙasa ya durƙusa a gabanta tare da riƙe ƙafafunta duk da kuwa shekarun dattijantaka sun bayyana a gare shi shima. Bata hanashi ba, sai kuka da take itama. Ga Ammar dake rungume da ita shima tuni kukan yake, dan a duniya basa ƙaumar ganin hawaye Dada da Mammah na ɗiga. Tsohon lokaci suna a haka kafin Mammah ta fara tsagaita nata kukan ta kama dattijon tana miƙarwa da faɗin, “Shike nan ya isa. Na yafe maka  ka share hawayenka. ALLAH ya yafe mana gaba ɗaya. Ya jiƙan Inna da Baba da Abdul-rasheed da Bashir. Received at 3:00 PMReac [01-16, 11:37] +234 703 449 6321: Amma dan ALLAH karka sake yin nesa da ni kaji”.        Tashi yay ya koma kan kujerar yana share hawayen nasa da faɗin, “In sha ALLAHU har abada bazan sake nesa dake ba Adda, na baya ma kunya ce da nadama ta sakani dole. Amma wlhy a kullum cikin begen son ganinki nake keda zuri'arki”.        “ALLAH ya rufa mana asiri”.   Mammah ta faɗa tana shafa kan Ammar alamar lallashi. Ɗakin ya sake ɗaukar shiru na wasu mintuna kafin ta kallesa ta ce, “Mi kake yi a Egypt? Ko nan kake aiki?”.         “A'a nazo ganin likita ne kawai. Yanzu ina Paris. Sai dai kusan shekara ma biyar kenan na koma ƙasarmu, kawai dai ina zaune a kudanci ne sakamakon tsoro da fargabar tunkarar ki.      Murmurshi Mammah tayi mai ƙayatarwa da faɗin, “Ja'iri ashe kana shakkata?”.          “Adda wlhy ina yi dan kece madadin Inna a wajena. Ya bayan rabuwa ya iyalai?”.       “To sai godiyar ALLAH, Iyalai kuma duk gasu nan sun girma sun zama magidanta. Duk da dai Bilal da Ammar da Biebah basu kai da yin aure ba. Amma Alhamdullah duk komai ya dai-daita babu abinda zamuce da UBANGIJI sai godiya”.         “Alhamdullahi naji daɗi sosai wlhy Adda. Kice yanzu gida ya cika da ƴan jikoki na”.       “A ya cika kam. Dan a ƙalla yanzu kana da jika goma sha bakwai zuwa sha tara nan gaba kaɗan, dan yanzu haka yau ɗin nan Mimi ma ta sake haihuwa ta huɗu. Matan Ma'aruff da Ja'afar ma duk suna da ciki a yanzu haka na uku-uku duk da ƙarami ne.”        “Kai Masha ALLAH lallai zuri'a ta haɗu. Ina yaron kirki Haysam?”.     Shiru Mammah tayi na sakanni, sai kuma tai murmurshi gajere da faɗin..........✍️ Received at 3:00 PMReac[01-16, 11:37] +234 703 449 6321: 16 ..........“Yana lafiya shima Alhamdullah. Kai fa ina fatan dai ƙanwata ta koma ko ka sake sabon aure?”.     Kansa ya ɗan shafa yana murmurshi, sai kuma ya ce, “Ta koma bayan taga na koma da kuɗin gidan nan, dan har mun sake haihuwar yara biyu ma. Amma ta rasu shekara kusan bakwai data wuce. Sai yaran yanzu kawai.” ya ƙare maganar idanunsa na tara ƙwalla. A take tausayinsa ya sake kamata. Ta shiga jajantawa da masa ta'aziyya. Shima Ammar yay masa ta'azziya. Dan har yanzu bai san ainahin wanene shi ba, tunda sanda wacan abun ya faru suna yara sosai musamman shi da Mimi ma da basu wuce shida zuwa bakwai ba maybe, sai dai ya fahimci ɗan uwan Mammah ne na jini koda kamanni da yanayin tattaunawar tasu.      Cikin share sabbin hawaye Tasi'u yake amsa musu. Mammah dai ta babbashi haƙuri daga haka ta koma jansa da hira harya saki jiki shima yana jan Ammar a jikinsa...... %><%><%><%><%>          Kwance take a madaidaicin gadon ɗakin daya kasance guda biyu iri ɗaya hannunta da waya tanata faman zabga murmushi, kai da gani kasan wani abu dake ƙayatar da ita take kallo. Dai-dai nan Ruky ta buɗe ƙofar bayinsu ta fito, ɗaure take da towel alamar wanka tayo, ganin yanda Nimrah ke zabga uban murmurshi bakinta har kunne yasa ta matsawa kusa da ita ta yarfa mata raɓar ruwankan dake ta bin farar fatarta.        Ɗagowa Nimrahn tai da sauri irin na firgita, dan haka Ruky ta ƙyalƙyale da dariya. Cikin harara ta kai hannu ya goge ruwan data yarfo mata ɗin ta ce, “Ƴar wulaƙanci miye na yarfa min ruwa?”.      Ruky na ƴar dariyarta har yanzu ta ce, “Gani nai kinata faman washe baki kamar ƴar tallar makilin, wai har yanzu hoton jaririyar kike faman kallo?”.         “Humm bazaki gane ba Ruky ALLAH jarirai nada ƙyan kallo, ina son jariri sosai, shiyyasa kike ganin duk sanda su Ammie suka haihu nake tarewa a sashensu. Ke nifa ko aure nayi duk shekara zan dinga hauhuwa”.       “Kambu, Ninah amma baki da hankali, duk shekara fa?”.     “Eh wlhy, ke ni ƴan bibbiyu ma”.   Zama kusa da ita Ruky tai da mai a hannu ta ce, “To ALLAH ya baki. Ni sai da kikai maganar haihuwa ma kika tuna min da sayyadi Kamal. Hummm bawan ALLAHn nan fa da gaske kamar yanda ƴan ajinmu ke gulma ya mutu a kanki Ninah, idan yana karatu hankalinsa duk a kanki. Ga kuma Teacher Khalil, yanda ya wani dage yana karemu randa muka suburbuɗi Hibba Abubakar na sake tabbatar da zancen Maimoon Qasim fa”.      Baki Nimrah ta taɓe tana gyara zama. “Ruky rabani da wannan shashancin kinji, ni wlhy duk basu min ba.”        “Kai Ninah kiji tsoron ALLAH, wlhy duk ɗinsu sun haɗu, dama dai kawai kice ba yanzu ba ne sai na yarda, dan mukace mun kawo samari yanzu ai ƙaniyarmu Uncle's zasu ci, musamman Uncle Bilal da akoda yaushe yake mana gargaɗin nan. Amma ALLAH nidai ina son soyayya, kinga idan naga Seniors ɗin mu na lobewar nan da boyfriends ɗinsu, ko mazan da ƴan mate ɗin mu sai naji kamar na bama Anwar ko Uncle Haneef ɗin gidan Mamy dama”.          “Lallai Ruky baki da hankali, yo ALLAH na tuba ko soyayya zanyi mi zan wani yi da ƴan tamatsitsin yaran school ɗin mu. Yo yaushe suma aka gama aikarsu kiran yayunsu gida. To ALLAH bari kiji, ko dariya naga kimma wannan Anwar ɗin sai na ci masa mutunci. Karki maida mu marasa aji mana, ƴan yara da su inama laifin kamar Yaya Ammar haka. Amma kosu Teacher Khalil nawa suke”.        “Hhhh shegiya Ninah, wato marasa aji? To yaushe ma muka gama tafasar balle mu ƙone har kike batun wani aji. Shekara sha biyar fa muke. Ga aunty Biebah nan harta kammala master ɗinta bata ma zancen aure, ta dage sai Dada ya dawo gida zatai aure. Hakama Aunty Ma'u dake ƙoƙarin kammala Secondary ita da Aunty Halimatu, balle azo kammu haihuwar jiya inji Yaya Mu'azz. Da kike kiran su Teacher Khalil yara kuma, ai bana jin Yaya Ammar zai girmesa. In baki so kamarsu ba tsoho kike so kamar su Daddy ko mi?”. Received at 3:00 [01-16, 11:37] +234 703 449 6321:        “Ƴar wulaƙanci, kamar su Daddy kuma? Kamar shekarun Uncle Ammar dai, amma kamar su Daddy ai da kunya ƴar soyayyar nan bazaka samu ka bajeta ba, kin san kuma nifa ina son harkar nan ta love ba wasa” tai maganar tana kashema Ruky ido ɗaya, bata jira cewar ta ba ta cigaba da faɗin, “Ya Mu'azz kam bar ɗan rainin hankali, shima sai kace ba haihuwar jiyan ba. Ya gama mana rashin m ɗinsa dai sai mun riga shi aure. Dan mu yanzu idan Daddy yace rana ɗaya za'a haɗa auren da Small Mom da su Aunty Ma'u mune next. Shifa, sai ya jira Uncle Bilal, Uncle Ammar da Yaya Khalifa ma ƙila, to ko Yaya Imam ya girmesa.       “A'a wlhy kar ki masa baki, duka shekara nawa Yaya Khalifa ɗin ya bashi, sai dai ayi musu tare, gara Yaya Imam to, kuma shima tare suke tafi a school ai”.     Cike da dariyar mugunta Nimrah ta ce, “Oho dai, ko haka ɗin mun more masa. Ke muyi gulma mana. Dan ALLAH baki ga wai kamar Uncle Bilal da Aunty Ma'u akwai wata a ƙasa bane?”.       “Humm wlhy na gani, ranar graduation ɗin su Small Mom sai wani kallon ƙasan ido yake mata.” dariya suka kwashe da ita harda tafawa. Nimrah ta ce, “Wlhy soyayya tayi Besty, idan ban samu ɗan soyayya ba na rako mata duniya”. Cikin dariya Ruky tace, “Muna son soyayya zaki ce, ai duk wanda yazo sai mun tantance shi walle karki damu, love ai duniya ce”. “A wlhy love duniya ce, shiyyasa nake son maƙalewa a sashen su Mamy, dan in ana bajakoli su da su Uncle's nasha kallona”. “Muguwa, wlhy Ninah kiji tsoron ALLAH, tun baki tafasa ba zaki ƙone. ALLAH yasa su ganoki suci ƙaniyarki, kinga sai ai miki auren ai”. “Shegiya ni da ke ai duk sammakal ne, zatace ta tadda muje mu”. Dariya suka sake fashewa da ita suna tafawa.....     Buɗe ƙofar ɗakin nasu ya saka su yin shiru, sai kuma duk suka rufe bakunan nasu da hannu. Biebah ta hararesu.        “Anya kuna duba agogo kuwa? Kuke mana irin wannan ihun dariyar haka kamar sabbin kammu”.       “Kai Mom ALLAH hira ce kawai tai daɗi”.      “Kuma da ihu haka? Na sake jin wannan dariyar kamar ba mata ba sai na ɓata muku rai. Dalla ku bani wayata kuyi shirin barci ku kwanta” tana gama faɗa ta amshi wayar tata da Nimrah ke kallon hoton baby, Dan su basu da waya Uncles nasu sunce ba yanzu ba. Juyawa tai ta fita tana mai rufe musu ƙofar. Gwalo sukai ma bayanta a tare, kafin Nimrah ta miƙe zuwa bayin itama dan yin wanka. Bata wani jima ba ta fito, lokacin har Ruky ta gama nata shirin barcin ta haye gadonta, dan kowa da nashi. Ƙasa-ƙasa suka cigaba da hirar a haka kuma duk ta sanari har Nimrah ta shirya itama ta haye nata gadon.        WASHE GARI da wuri suka ta shi, babban burinsu tafiya gidan Aunty Mimi ganin baby musamman ma Nimrah da jiya ba'aje da ita ba. Dan tana barci su Aunty Shariffa suka wuce da Ruky, sai yau Biebah tace zasu je tare tunda itama bataje ba taje Tahafiz, amma tace mata yau ma sai sunje sun dawo daga Tahafiz suma sannan. Rashin sabon barcin safe saboda makaranta yasa suna kammala salla sukai bitar karatun Alkur'ani dan sun san yau sayyadinsu zai amshi hadda sukai azkar kowa ya miƙe. Ruky ta fara gyara ɗakinsu ita kuma Ninah ta wuce gyaran ɗakin Biebah. Koda ta shiga ɗakin Biebah harta sauka ƙasa taya masu aiki haɗa breakfast ita kuma. Sun kammala gyara ɗakuna har bedroom ɗin Mammah duk da bata nan basa gajiya da gyarawa sannan suka shiga wanka. Dama bedrooms suke gyarawa da sama ɗakin su Yaya Ammar, sauran wajaje kuma masu aiki. Shirin sukai cikin uniform ɗin islamiyya su ash color na wando da hijjab har ƙasa tsahon hijjab ɗin yasa da yawansu basa yin rigar suke saka t-shirt a ciki. Fitowarsu dai-dai da fitowar Biebah daga nata ɗakin tana wani kalar sassanyan ƙamshin turare. Su duka kasa haƙuri sukai sai da suka tanka.       “Woow Small Mom kin sayi sabon turare ne? Wlhy wani ƙamshin bala'i mai kassara jiki”.       Murmushi tayi tana ɗan girgiza kanta. “Yan biyun Mammah kenan iyayen iyayi ƴammatan gobe. To wannan ƙamshin da kuke ji ba turaren kanti bane, haɗaɗen turaren gida ne dan khumra ce ma kawai na ɗan shafa sai kabasa da nayi a kaya na, nima a sashen Aunty Lailah na samoshi. Received at 3:00 PMReact[01-16, 11:37] +234 703 449 6321: KIƊA A RUWA 17 .......Gaba Biebah tayi tana musu dariya, dan in dai halayen Twins ɗin gidan nasu ne tafi kowa sabawa. Suna sakkowa dining suka nufa, Mu'azz ne kawai zaune yana kari shima sanye da uniform ɗin islamiyyar. Cike da neman magana Ruky ta ce, “Su Yaya yau kuma da yunwa aka tashi?”. Harara ya wulla mata, batare daya tanka ba ya cigaba da danna doyarsa a baki. Nimrah tai dariya tana zama a kujerar kusa da shi. “Kaga rabu da ita Yayana. Kasan ita Ruky wani lokacin uwar gulma ce. Ina kwana”. “Ai ke da ita duk sammakal. Wannan saurin gaisuwar bana ALLAH bane faɗa min nawa kike so?”. Dariya Biebah da Ruky suka sanya. Cikin ɓata fuska da tura baki Nimrah ta ce, “Kai Yaya sai kace wata mayyar kuɗi, kai shike nan bazamuyi shirin arziƙi ba sai ina son kuɗi”. “A to nasan halinki ne ai Ninah”. Tashi tai a kusa da shi ta canja kujera, ya ce, “Oho dai”. Bata kula shi ba, dan dai-dai nan ma su Abees suka shigo da gudu suma sanye da irin uniform ɗinsu. Tuni Nimrah ta miƙe tana faɗin, “Oyoyo my Afry”. Ai ko da gudu Afrah tai kanta, ta ɗagata sama tana juyi da ita suna dariya dan ƴar gidanta ce. Su Aheel kuwa wajen Ruky da Biebah da Mu'azz sukayi suma. Nan fa surutun falon ya ƙaru, dan bayan yaran sun gaishesu suma duk zama sukai Ruky ta saka ma kowa abinci a gabansa. Sai da Biebah ta tsawatar ma surutun basu sannan sukai shiru kowa ya maida hankali ga abincinsa. Shaf-shaf suka kammala suka fito karsu makara. Yau sabon driver ɗin su ne zai kaisu. Wanda suna haɗa ido da shi yau ma gaban Nimrah ya faɗi, dan haka ta kauda kanta gefe tana gaishe shi kamar yanda su Biebah ke gaishe shi. Dan ba yaro bane. Gaba Mu'azz ya shiga shi da Abees da Aheel. Su kuma ita da Ruky da Biebah suka shiga baya, sai Afrah da Ayyan tare da su. Mu'azz ne ya dinga nuna masa hanya har suka iso. Islamiyyar su babba ce sosai, dan harda securitys. A inda ya dace yay parking duk suka fita. Karaf suka haɗa ido da Nimrah, yanda tsigar jikinta ta wani tashi sai da ta ambaci hasbunalahu wani'imal wakil a zuciyarta. Da sauri ta kama hannun Afrah suka bar wajen. Shima kansa ya kauda yana maida idanunsa kan Mu'azz. “Ɗana zan tafi ne ko zan jira ku anan har ku fito?”. “A'a Baba zaka koma gida, sai ƙarfe ɗaya kuma in sha ALLAHU sannan an tashi su Ayyan kazo ka ɗaukesu mu kuma ka taho mana da abinci, sai anyi la'asar kuma ka dawo ka ɗauke mu.” “To to ba damuwa ALLAH ya nuna mana”. “Amin ya rabbi, zadai ka gane hanya ko?”. “Sosai kuwa, karka damu zan gane. Ai na taɓa aiki tanan wajen sosai dan nayi taxi”. “Oh ALLAH sarki, shike nan sai an jima ɗin to baba”. Daga haka shima Mu'azz ɗin yabi bayan su Nimrah da tuni sun shige..... }}}{{{{}}}}{{{{ “Alhamdulillah Sir! Yanzu kam komai ya kammala kenan, sai jiran umarnin fara campaign”. “Haka ne Imran, amma ni duk ma jikina yayi sanyi. Badan al'amarin Haysam ba banga abinda zai kai ni shiga siyasa ba. Dan siyasar ƙasar nan sirrikan cikinta basu da daɗin tonawa. ALLAH dai ya rufa mana asiri ya ƙara kare mana imaninmu”. “Amin ya rabbi Sir. Amma abubuwan dama ko ba'ace komai ba duk mai hankali yasan akwai ɗunbin kwamacala a ciki kam. ALLAH dai ya kare mana ku, ya azurtamu da shugabanni na gari.” “Iyakarta kenan kam. Mu dai ku cigaba da mana addu'a, ku dinga saka yara na mana.” “In sha ALLAHU Sir za'a ƙara dagewa, dama anayi a koda yaushe. Sir nace yanzu bazaka sake sama mana damar ganawa da Haysam ba. Wlhy ina cikin matsanancin matsin zuciya na kewarsa matuƙa. Shekara biyar ba kwana biyar ba”. Sosai tausayin Imran ya sake cika zuciyar Janar, dan har idanun Imran ɗin sun cika da ruwan hawaye. Cikin kwantar da murya ya ce, “Kayi haƙuri Imran, na san kai da zuri'ar Haysam da iyalinsa dole ne ku kasance cikin bege da kewarsa. Kuma hatta muma muna cikin wannan yanayin. Amma ina sha ALLAHU aski ne yazo gaban goshi, kasan kuma masu iya magana sunce daman yafi zafi. ReceivedDole ne mu cigaba da daurema zukatanmu, dan wannan gaɓar da muke da babban shiri a kansa tafi kowace gaɓa nauyi da haɗari, idan mutanen nan suka fahimci muna da wani shiri wlhy zasu iya kashe Haysam ta guba da hanyoyi masu sauƙi dan a yanzu sun fimu kusanci da shi. Mu cigaba da masa addu'a kamar yanda muka saba, tunda muna samu labari mai daɗi akan kasancewar sa cikin koshin lafiya daga yaron nan Captain Ibrahim, na yarda da yaron bazai kawo mana zancen daba haka yake ba, muma shaida ne tunda ya kawo mana wasiƙa da muka tabbatar daga Haysam take. In sha ALLAH ko ban samu mulkin nan ba a wannan karon zan ƙara ƙaimi Imran”. “Maganarka haka take Sir, kayi haƙuri nima kewa ce da damuwa harta sani faɗar hakan. ALLAH ya saka maka da alkairi ya bada ladan zuminci.” “Karka damu Imran, wlhy har cikin zuciyata nake jinku kai da Haysam da Haydar, dan naji matuƙar daɗin aiki da ku fiye da yanda kuke tunani. Shiyyasa nake jinku tamkar ƙannena da muka fito uwa ɗaya uba ɗaya. Zan iya bada rayuwata akan ganin Haysam ya fita, dan ya yimin abubuwa da bazasu ƙirgu ba. Sau biyu Haysam na tarar harsashi a wajen bani garkuwa, kuma duka biyun a jikinsa suka ƙare har yay jiyya. Taya zan manta da irin wannan ƙanin a duniyata in dai ina numfashi.” Hawaye Imran ya share yana ɗan murmurshi, ya ce, “Ka cancanci fiye da haka a wajenmu Sir. ALLAH dai ya ƙara lafiya da nisan kwana mai albarka, ya kuma cika burin alkairi”. Sun cigaba da hira da duk ta shafi batun Dada da siyasa. Kafin Imran yay masa sallama ya fito. Da yake cikin ɓadda kama yake maimakon gida sai ya ɗauki hanyar kasuwa, dan jiya Mimi ke sanar masa haihuwar ta, yanzu haka ma ya bari Aunty Hafsat zata je can barka. Wani shago ya fara shiga, sai da ya tabbatar babu mai bin bayansa daga gidan Janar sannan ya fito ya nufi babban shagon su Ma'aruff da yafi kowane shago girma da cikar kaya a kasuwar. Dan kuwa ƙaton waje ne da zaka iya samu abubuwa da yawa da duk ya shafi kwalliyar jiki. Ɓangare-ɓangare ne, akwai atamfofi, abayas, lesuka, shadda, materials, kayan yara tun daga kan jarirai har zuwa samari. English wears na mata dana maza, mayafai. Kai duk wani abinda ya shafi sutura ta maza da mata, yara da manya akwai ta. Sai bangaren kayan kwalliya, akwatina, cosmetics komai har zinari suna sayarwa. Kai shagon nan dai sai Alhmdllh, dan ko yara masu aiki sunfi ashirin a ciki. Suko manyan gwasake na office abinsu. Ga camaras tako ina da suke kallon shiga da fitar kowa daga ofisoshin nasu... A tare ma ya taddasu a office ɗin Ja'afar, dan sakatariyansu batama yi yunƙurin fara zuwa neman masa izinin shiga ba sanin wanene shi a wajensu. Sai ma gaisheshi data shiga yi cike da girmamawa. Ya amsa mata a taƙaice yana wucewarsa yay knocking direct, sannan yay sallama ya shiga. Cike da farin cikin ganinsa da girmamawa suke masa barka da zuwa. Ma'aruff ya ajiye kofin tea ɗin hannunsa da yake sha yana miƙewa ya gyara masa kujera, dan basuyi breakfast a gida ba saboda sun makara aka haɗa musu suka taho da shi. “Cin abinci a office sai kace tuzurai?”. Imran ya faɗa cike da tsokana. Dariya sukayi a tare. Ja'afar ya ce, “Yaya makara mukayi wlhy, kasan kuma twiny da wutar ciki ya azalzalan dole muka taho da shi. A haɗo shayi ko coffee ko kunu?”. “Haba sai kace wani ku, sai da Auntynku ta cika min ciki na fito nikam. Bani ruwa mara sanyi kawai it's okay”. Ja'afar na dariya ya kawo masa ruwan, da kansa ya zuba masa a kofi sannan ya zauna suna gaishe shi a tare. Da kulawa ya amsa musu, da faɗin, “Gobe su Mammah zasu dawo ko?”. “In sha ALLAHU Yaya, wlhy duk kewarta ta ishemu gidan ba daɗi. Autocinta ma duk sunyi sanyi ko ƙiriniyar basa yi da ƙyau kwana biyu”. “Ai ni kaina kewar tata nake. Jiya da safe dana leƙa gidan duk sai yay min wani iri. Dan itama Ammah ta maƙale a ƙauye taƙi ta dawo Abbah nata ƙorafi”. Received at 2:05 PMReactions Cikin dariya har suna haɗa baki wajen faɗin, “Ai jiya da muka je da daddare yanata faɗa, wai yau tunda safe zai aika driver a ɗakkota, shi ya gaji su Mabruka nata bashi kwamacalar abinci, tuwon ma jiƙaƙƙe suke masa”. Yanzu kam dariya suke harda Imran. Dan rikicin Abba sai Hajjo ke iya masa. Itama idan ya rikice mata wani lokacin sai ta haɗa shi da Mammah da yake ɗauka tamkar babbar ƴarsa ake samun lafiya. Sun cigaba da hirarsu har suka gangaro kan batun Bilal da shima dai watan gobe zai dawo gida in sha ALLAHU. Sai magana auren Biebah data dage ita bazatai aure ba sai Dada ya fito, in ba haka ba ita da aure har abada. Imran da yasan ga shirin da suke yace su barta kawai in sha ALLAHU komai zai warware. Bai bari shagon ba sai bayan sallar azhar. Ya haɗo shopping na kayan babys da turamen atamfa har akwati biyu aka kai masa mota. Gida ya wuce kai tsaye, zaije ya ɗan samu ya huta bayan la'asar sai ya leƙa gidan Mimi yaga baby dan dama siyayyar duka tata ce......✍️ Received at 2:05 PMReactio [01-16, 11:37] +234 703 449 6321: KIƊA A RUWA 2 18 .........Sai da sabon driver ya tabbatar su Nimrah sun gama shigewa sannan ya koma cikin mota. Wayarsa ya ciro daga aljihu ƙarama tecno, ya kashe ta ya cire murfin da batteryn ta. A mamakina rigarsa ya ɗan ɗaga ya zaro leda mara girma sosai, koda ya kwance ta tsumma ne fari ya fara bayyana da aka nannaɗe wani abu a ciki. Ya shiga warware tsumman sai ga ƙaramar bindiga ta bayyana, ƙaramar takardar dake tare da bindigar a nannaɗe itama ya ɗauka ya warware layukan waya da yawa suka bayyana. Ɗaya a ciki ya ɗauka ya saka a wayar ya maida batteryn ya kunnata. Kira yayi tare da kaita kunensa yana gyara zama. Ba'a wani jima ba aka ɗaga daga can. Kasancewar speaker ɗin wayar a buɗe take sosai yasa ake iya jin abinda nacan ke faɗa. Gaisuwa suka fara kafin nacan ya cigaba da faɗin. “Ai harna fara tunanin sakawa a bi bayanka Mole, naji har kwanaki uku babu wani bayani daga gareka. Ina fatan dai lafiya? Ka samu karɓuwar da muke so a gidan?”. Iska mai ƙarfi ya furzar cikin damuwa da ɗacin da yake ji a cikin maƙoshinsa ya furta, “Oga na samu ƙarɓuwa kam, sai dai akwai matsala gaskiya.” “Matsala kuma? Yarinyar bata tare da su ne?”. “Tana nan a gidan. Ta girma sosai ta zama budurwa. Sai dai babu wata alamar dake nuna tasan tana da wasu iyaye bayan su. Da alama abinda Goje ya taɓa sanar mana na an mantar da ita iyayenta gaskiya ne.” “Amma uwar nan tata muguwa ce gaskiya. Tabbas da ace tana raye har yanzu ba ƙaramin barazana zata zame mana ba ita da ubanta.” “Ai ko yanzu ta zame mana, dan ban san ta inda zan fahimtar da Uwa wanene ni ba har tai mana abinda muke buƙatar daga ƙarshe ta dawo hannuna”. “Karka damu dole mu tafi mataki na biyu ne kawai gaskiya. Amma ka bari zan yi magana da oga muji wace shawara ko shiri yake da shi akan hakan. Tunda dama ya kamata mu sanar da shi da kanka zakai aikin yanzu, dan kar a samu irin matsalar da Buba yaso bamu. Yanzu a gidan kake kwana?”. “A'a haba kaima kasan bazan kwana a nan ba. Dan wannan Imran ɗin da kuka raina shima shegen kansa ne. Tunda ya ganni alamun tsarguwa suka bayyana akan fuskarsa. Dole sai nayi taka tsantsan da shi. Dan ni kasan bana raina abokin gaba”. “Kamar ni kake, dama su Oga ne ke ɗaukar Imran mai sauƙi, sun kasa fahimtar irinsu sunfi illa fiye da shi wanda suka ɓoye ɗin da bai iya shanye abu. Amma ka barsu za'aje gaɓar da zasu gane shima ba abinda zasuyi wasa da shi bane. Kai kuma ka ƙara yin taka tsantsan”. “Ba damuwa sai na jika”. Daga haka sukai sallama ya sake kashe wayar ya cire layin ya maida shi inda yake tare da bindigar nan. Sannan ya tada motar yabar wajen..... (Hummm wa kuke tunani wai?) }}}}}}}}}{{{{{{{{{ ★PRISON★ Bai san fuskar ba, bai taɓa ganinta ba. Dan haka ya zubama vistor ɗin nashi jirkitattun idanunsa masu bulale abokan gaba koda bai tanka ba har na tsayin minti ɗaya. Tabbas ALLAH ya bama Dada basira mai ƙarfi, nutsuwa, dattako da sirrin iya aiki matsayin jami'in tsaro. Zakai matuƙan shan mamaki idan akace maka a wannan kalon na minti ɗaya kacal ya fahimci fuskar bogi ce a tare da mutumin, hakan na nufin yayi amfani da facemask wajen ɓoye ainahin fuskarsa. Wani murmushin da sam bai niyyasa bane ya suɓuce masa, murmushi daya saka vistor ɗin nashi murmusawa shima, duk da bai fahimci ma'anar murmurshin Dadan ɗin ba shi. Shiru ya sake biyo baya a cikin ɗakin batare da yunƙurin tankawar kowannensu ba na tsawon lokaci. Tamkar Dada na ƙirga lokutan zamansa a wajen ne, minti biyar na cika daga agogon ɗakin da suke ya miƙe tsam batare da yace komai ba ya juya zai bar wajen. “Bai kamata ka ƙosa haka da wuri ba, domin mu mutuwa ne, ana rayuwa da mu ne dole, tun daga ranar haihuwa”. Cak Dada ya tsaya a takunsa na uku, sai dai bai juyo ba bai kuma ce komai ba har tsahon minti guda cir. Kafin a hankali cike da ƙasaitarsa mai tafiya da nutsuwar masu izza ya juyo gaba ɗayansa. Idanun nan nasa masu kaifi da zafi ya zuba masa, kafin a bazata yay wani sakaran murmurshi mai cike da ma'anoni masu ƙarfi da ya nema tarwatsa zuciyar vistor ɗin a cikin ƙarjinsa. Received at 2:05 PMReactions:Ya lumshe idanu ya sake buɗewa a kansa. Sai kuma ya buɗe lips kaɗan, gira a sama ya amsa masa da. “Ni kuwa kaga anan sai banga siffofin kamala irin na mutuwa mai cika umarnin UBANGIJINA ba. Siffofin akuyoyin dake gudun tsiran neman mafaka a yayin da ruwan sama ya sauka kawai na gani a gabana”. Sosai fusata ta nuna a fuskarsa vistor ɗin, duk yanda yaso danne fusatarsa hakan na neman gagara. Idanunsa sun yi ja sosai har hannunsa na rawa sai da ya dunƙuleshi a cikin juna ya matse yatsun. Dada dake kallon hannun nasa ya kauda idanunsa yana murmurshi. Ai ko sai hakan ya sake hasalashi, a kausashe ya daki tebirin yana furta, “Mune akuyoyin kenan?”. “Amsa mai ƙyau”. Dada ya bashi amsa kai tsaye yana sake takowa ya dawo wajen. Duk da hannunsa akwai handcuffs cike da salon manya ya juya kujerar ya zauna ƙafa ɗaya kan ɗaya suna kallon juna ido cikin ido. Dai-dai lokacin masu tsaronsa suka shigo saboda bugun teburi da baƙo yayi. “Sir! are you all right?”. Kansa kawai ya jinjina musu batare da ya kallesu ba balle yin magana. “Okay”. Suka faɗa suna salute ɗinsa da ɗan kallon baƙon da ya gama kaiwa wuya suka fice. Sai kuma ga wasu sun sake shigowa niƙi-niƙi da kwalaye. Su kam gaisheshi sukai kawai tare da sanar masa oga ne ya aikosu da kayan zasuyi aiki a ɗakinsa. Kamar zai ce wani abu sai kuma yay shiru da basu dama da hannu suka wuce ɗakin nasa. Ya ɗan bi kwalayen da kallo. Har sai da baƙon nasa yay wata dariyar iskanci da izgili. A wulaƙance ya ce, “Karka ji ka damu fa, mun ƙara maka matsayi ne, dan bai ƙyautu ace lokacin da mutanenka ke ihu da kururuwa kai kunnenka baya ji ba, idanunka basa gani ba. Shiyyasa muka kawo maka gift ɗin da zai baka damar ji da gani kusa da kai gab...” Tsahon sakanni bashi da niyyar tankawa daga kalamansa, sai hakan ya bama vistor damar taɓe baki da sake faɗin, “Kana jin tsoron rasa rayuwa ne? Ko faɗa ka bada amsa ne kake jima fargaba?”. Da wani irin salon luuu Zak-Dada ya ɗago idanunsa yana kallonsa cike da izza da nutsuwarsa da ALLAH ya mallaka masa a kowane hali. Sai kuma ya ɗan matso kaɗan ya dafe duka hannayensa dake sanye da handcuffs a saman table ɗin, idanunsa ya sake ajiyewa kai tsaye cikin nasa tamkar zai soke ruhinsa da su. Da golden voice ɗin nan tasa mai razanasu ya furta, “Jarumin gaske sulƙen yaƙi da linzamin dokinsa ne kawai GUZIRINSA. Duk lokacin da kaji abokin faɗa ya zagaye kansa da MAKAMI ni Haysam Abdul-rasheed Shehu Kobi na faɗa maka tsoro ne ya saka shi”. “Tsoro!?”. Baƙo ya faɗa cike da son aro jarumta da ƙarfafa kai na dole. Sai kuma ya murmusa yana ɗan buga yatsunsa akan tebur. “Kana da yawan cika baki a magana. Amma ka sani mu ba da suna muke aiki ba. Idan suna ya bayyana, haske zai shigo. Idan haske ya shigo, tsarin ya lalace. Mu mune mazaunan ƙasa a ɓoye. Mu ne masu murɗa jijiyoyin gwamnati. Mu ne masu rubuta dokar da gwamnati ke karantawa.” Ya sake matsawa kusa kusa sosai. “Yau shekaru takwas kenan muna kallonka daga nesa. Kana tunanin wannan gadarar taka ce ta baka wannan filin? Ko har yanzu gurɓataccen tunaninka na cigaba da baka wancan ƙarfin ikon da kake gadara da shi a baya har yanzu yana da tasiri? Ka manta cewa ƙasar nan tun kafin ka yi tunanin kare ta, mun riga da mun shafe shekaru muna sarrafa zuciyar manyan da kake kira shugabannin cikinta. Kalli kanka mana, har yau baka ɗauki darasi daga ikonmu bane?. Mu muka bar ka a nan. Mu muka hana a kashe ka. Mu muka hana a sake buɗe shafin ka. Ba wai saboda kana da muhimmanci a garemu bane. A’a…” Ya yi kakkarfan numfashi yana wani murmushi, ya cigaba da faɗin, “…saboda muna son ka zauna ka kalli yadda ƙasar da ka ɓata shekarun ƙuruciyarka a kareta ta koma filin WASAN ƘWALLON ƙafarmu. Da jinin abokanka, zuri'arka, ƴan ƙasar taka zata zame mana mai danshin da zamu ji daɗin gudu a kanta. Kaɗan da zamu rage a cikinsu ka kalli yadda suke bauta mana. Ka kalli yadda za mu rusa duk tsarin da ka kare rayuwar taka a karewa. Ka bar gudanar da tunanin cewa kai ka san makircin ƙasa. Received at 2:05 PMReactionsKai ɗan wasa ne a wani katafaren wasan da muka fara shekaru masu yawa da suka wuce tun kan haihuwarka, kaga hakan yayi kama dana masu TSORO?”. Ya ƙare dogon sharhin nashi yana gyara zama da jifan Dada da kallon raini yana wani dariyar iskanci da izgili. Sai dai maimakon yaga Dadan ya firgita ko nuna tsorata da matsanancin tashin hankali kamar yanda sukai tsammani sai yaga saɓanin hakan a bayyane. Domin kuwa da wata nutsuwa da baƙon bai taɓa gani ba, ya ɗaga kansa ya kalle shi da idanun da suka saba ganin bala’i ba tare da girgiza ba.........✍️ A gaya masa gaskiya ko a barshi da Dadan kai?. To bari dai mu gaya masa ko kaɗan ne 😂💃. 😝Kai kam baƙo duk wanda ya baka shawarar zuwa wajen nan ba sonka yake ba, yo ubanwa ke zuwa gaban zaki yay wasa ya kwashe kayan wasan salin alin ya koma gidansu yay barcin hutu.🥱. Amma dai bari muji amsar da MAZAN FAMA zasu baka🤣. Barkanmu da dawowa, ya weekend?😎 Received at 2:05 PMReactions:[01-16, 11:37] +234 703 449 6321: KIƊA A RUWA 2 19 .........Ana fitowa sallar azhar driver ya kawo musu abinci da ɗaukar su Aheel. Babu yanda Ruky bataiba suje su amso Nimrah taƙi, dan ita kam haka kawai ganin mutumin nan tayar mata da hankali yake ta rasa dalilin haka. Tana zaune a inda Ruky ta barta ta dawo ta sameta. Tana ma buɗe abincin ta sake ɓata fuska ganin minene a ciki. Dariya Ruky tayi, dan tasan Nimrah bata damu da doya ba sam. Harararta tayi kuwa, ƙarshe ta miƙe wai ita ta ƙoshi bazata ci ba. Sanin butsutsunta yasa Ruky bata takura mata ba, anan ma ta barta ita ta koma aji. Sai da taci iya abinda zata iya ta rufe sauran ta koma ajin itama. Sun cigaba da ɗaukar darasi, Nimrah nata mutsu-mutsun yunwa, gaba ɗaya sai Ruky ta damu, har cikin ranta taji haushin su Kulu da suka aiko musu da doya bayan sun san Nimrah bata ci. Jakarta ta ɗakko ta ciri kuɗi tare da miƙewa taje gaban sayyadinsu cikin ladabi ta sanar masa zata fitsari. Bai hanata ba dan hakan normal ne. Tana fita maimakon restroom sai ta wuce shop ɗin makaranta. ALLAH ya taimaketa ta samu sauran meatpie bai ƙare ba ta amso mata biyu ta dawo tunda suna da ruwansu. Sai da ta zauna sannan ta saka mata a hijjab. Kallonta Nimrah tayi, sai kuma ta tattaɓa abinda ta ajiye mata akan cinya. Wani irin ƙaunar Ruky ce ta sake cika mata zuciya. Idanunta cike da ƙwalla ta ce, “Thanks you Sweetheart”. A hankali. Murmushi kawai Ruky tai mata. Cikin hijjab ta shige tana ci, duk da kuwa hakan doka ne ba'a ciye-ciye a aji. Amma da yake Sayyadi Kamal nada wani ƙudiri a ransa game da Nimrah ɗin duk da ya fahimci abu take ci baiyi magana ba. Haka ta kammala tasha ruwa sannan ta fito itama ta maida hankalin ta a karatun. Ya kammala ya fita wani malamin ya shigo, haka dai har lokacin tashi yayi. Yau dai sambarka ƴan caskalen Mammah basuyi faɗa da kowa ba. Abinda take ji aduk sanda suka haɗu da driver yasa tai juriyar ƙin kallonsa a yanzu har suka isa gida. Ita ta fara fita ta shige ciki. Baƙar yunwar da take ji ya sata wucewa kai tsaye kitchen tace su Kulu su dafa mata noodles da ƙwai soyayye ɗaya. Kafin ta shige ɗakin su. Ruky na kwance a gado tana maida numfashin gajiya, dan haka ita bata zauna ba sai ta wuce bathroom kawai yin wanka. Kafin ta fito kuwa an kawo mata indomie ɗinta har Ruky na ƙoƙarin ɗanɗanawa. Doke mata hannu Nimrah tai tana ƙwacewa, Ruky ta lunƙuma wadda ta ɗiba a baki tana dariya da faɗin, “Shike nan ke in kina jin yunwa sai baƙar rowa”. Cike da jin haushi ta bata amsa da, “Ai sai na musu rashin mutunci yau a gidan nan, sun san bana cin doya sukayi, maimakon su dafa min wani abun”. Ta ƙare maganar da ƙwafa idanunta na cika da ƙwalla. Dan harga ALLAH taji haushi, sai dai bata san miya hasala zuciyarta ba kuma har kamar haka. Itama Ruky ta fahimci a hasale Nimrahn take dan haka batace komai ba ta wuce bayi tana murmushi... Shaf-shaf suka kammala shirin zuwa gidan Aunty Mimi. Sunyi ƙyau cikin abaya iri ɗaya kalar brown da adon duwatsu masu haske. Daga Ruky har Nimrah akwai son kwalliyar tsiya. Ga iyayi kuma da ƴammatanci kamar ba ƙwailoli ba😝🏃🏼‍♀️. Koda yake sunce su ba ƙwaila bane ba😂, dan duk abinda cikakkiyar budurwa ke taƙamar da shi suna da. Fes suka fito abinsu, kai tsaye ɗakin Biebah suka shiga, itama dai ta shirya cikin nata gayun, sannin turaren SHUWA INCENSE AND MORE +234 704 229 3387 suka biyo ya sata ɗauke kwalbar tana ƴar hararsu. “Kai waɗan nan yara baƙwa mantuwa”. Dariya suka kwashe da ita a tare, Ruky ta ce, “Humm Small Mom ya zamu manta da wannan daddaɗan turaren, ai kafin a kawo mana namu muma sai su Ammy sun ɗiba mana komu sato”. “Ai dama kun saba ɓeraye”. Dariya suka sanya a tare nan ma. Ta daddagwala musu kowa ya shafa suna faman lumshe idanu. Dan ƙamshin turarrukan ba ƙaramin ratsa zukatan mai shaƙa suke ba. (Nima shaida ce masu karatu. Wlhy maza ku garzaya neman turarrukan SHUWA INCENSE AND MORE +234 704 229 3387. Kaf turarrukanta babu na yarwa, nayi amfani da su na gani, koma nace ina kan yin amfani da su a yanzu haka. Tana kawo turarrukanta ne masu inganci da tsaftatacen ƙamshi. Received at 2:05 PMReactions:Akwai Turare wuta da khumra kaloli har uku: black khumra, white khumra, brown khumra. Akwai oil perfume da kullacham ma, akwai Genine da Turare kabasa kaloli uku shima: white, black, and brown kai harma abinda ban lissafo ba. Dan tana saida kayan gyaran jiki suma na amare dama mata ƴan ƙwalisa uwargidaye masu san gyaran fata batare da kin ɓata skin ɗinki da mayukan bleaching ba. Karku ji komai ta gida ce tana nan zaune a garin Kaduna kuma tana aika kaya aduk inda kake harda kasashen ƙetare ma. Duk mai so kawai ya nemeta ta nan. Tana bada har sari ma fa masoya. +234 704 229 3387😌💃🏼🥰👍🏼). “Kai kuko wane kalar ƙamshi kukeyi haka? ya subahanallah”. Mu'azz ne mai maganar yana faman buɗe hanci. Dariya Ruky da Biebah sukayi, Nimrah kam da duk take jinta cikin rashin daɗin zuciya murmurshi kawai tayi. Ganin haka yasa Mu'azz kallonta, cike da kulawa ya ce, “Yaya dai Ninah? Ko baki da lafiya ne? Naga tunda muka baro makaranta baki da walwala”. Kai kawai ta girgiza masa alamar ba komai. Bata basu damar magana ba ta ce, “Ku muje ALLAH na ƙagara naje naga Baby”. Tana gama faɗa ta fice a falon gaba ɗaya. Duk da kallo suka bita suma fuskokinsu na nuna damuwar. Koda suka iskota a waje babu wanda yace komai, kasancewar Mu'azz ne zai jasu sai ta sauke ajiyar zuciya. Ita ta shiga gaba Ruky da Biebah na baya. Su Afrah dama suna can, dan daga makaranta can driver ya kaisu kai tsaye. Koda maigadi ya buɗe musu gate bata ganshi ba, dan haka ta sauke ɓoyayyar ajiyar zuciya. Suna ɗaukar titi kowa ya fara mata tambaya, saita wayance tace kewar Mammah ce. Duk sun gamsu, dan sun san Nimrah da Mammah sai ALLAH. Nimrah akwai ƙulagucin iyaye, dan haka tai bala'in sakin jiki da Mammah duk da har yanzu bata manta da Ummanta ba, sai dai bata iya tuna fuskarta sosai saboda ƙarancin shekaru na wancan lokacin. Tunda ta fara hankali da wayo cikin hikima Mammah ta koyar da ita yima mahaifanta addu'a kwanciyar kabari cikin aminci. Kulawa da take samu yasa bata jin maraici, ba kuma ta taɓa zaman yin kukan rashinsu ba sakamakon babu wani abu na labarinsu data sani ko take ji a yanzu balle ya tuna mata abubuwa a kansu. Garama Ummanta wasu ƴan abubuwan kan mata flash ɗin baya game da ita a cikin zuciya musamman idan Mammah ko su Aunty Ummi da zasu iya zama sa'annin Umman ita da Ammie (Aunty Hafsat mahaifiyar su Ruky kenan Matar Imran) takanji kamar Ummanta. Suna isowa tun Mu'azz bai gama kashe motar ba ta fita da gudu tai cikin gidan. Dariya kawai sukai mata. Aunty Biebah na addu'ar ALLAH ya cika musu burinsu na fitowar Dada sarari wataran Nimrah ta haifa musu Baby gudan jinin sa. Ita kanta bata san yanda zata misalta irin farin cikin da wannan ranar zatazo musu da shi ba balle Mammah.... “Oh ya ALLAHU ka shirya min Ninah jama'a ke da wa?”. Zama Nimrah tai kusa da Aunty Mommy dake rungume da Baby tana saka masa kaya an mata wanka tana murmushi, sai da ta shafa kan babyn sannan cikin shagwaɓa ta bama Aunty Momyn amsa. “Mum ba kowa fa, kawai ina gudu na fara ganin Baby ne. Jiya fa dan mugunta Ruky ina barci taƙi tada ni suka taho”. Aunty Mimi data kasa haƙuri ta ce, “Ai Dada zai sha fama a wajen nan dai kam. ALLAH yasa sanda zai dawo kinyi hankali Ninah”. “Mamy shi Dada ina ruwansa da hankalina koda ya dawo? Kuma ALLAH inada hankali”. Kasa haƙuri sukai kowa sai da ya dara. Ita kam ko'a jikinta tunda ta samu ta amshi Babyn gaisuwa ma sama-sama tai musu ta koma gefe. A haka su Biebah suka shigo niƙi-niƙi da kaya suna sanar da zuwan Daddy Imran. Dai-dai lokacin kuma Aunty Hafsat ta fito daga bedroom ɗin Aunty Mimi da alama salla tayi. Ai ko zaram Nimrah ta miƙe ta nufeta tana faɗin, “Ammie na dan ALLAH Babyn nan kalleta da ƙyau dawa take kama?”. Dariya Aunty Hafsat tayi ta ce, “Da ke. Sai dai ALLAH yasa kada tayo ƙiriniyar taku ke da hassanar ki”. Received at 2:05 PMReactions: Aunty Lailah dake fitowa a kitchen ita da Aunty Shariffa sai ƙanwar mijin Aunty Mimi ta ce, “A'a gara dai ta biyo komai da komai zaifi armashi Aunty”. Nan ma dariyar aka shiga yi, a haka Imran ya shigo ya samesu. Sai da ya zauna kowa ya gaisheshi cike da girmamawa sannan ya dubi Nimrah data ƙanƙame Baby bata da niyyar bayarwa. “Daughter baza'a bani Babyn bane?”. Murmushi tayi har haƙoranta na bayyana, sai kuma ta miƙe ta je gabansa tana faɗin.........✍️ Received at 2:05 PMReactio [01-16, 11:37] +234 703 449 6321: KIƊA A RUWA 2 20 .......“Daddy ai kaine za'a baka. Amma minti biyar zatayi ka sake bani. ALLAH ji nake kamar kada na ajiyeta fa. Daddy dan ALLAH na dawo nan da zama har ayi suna?”. “To Nimrah in kin dawo makarantar fa?”. “ALLAH Daddy in ta dawo nima sai na dawo”. Ruky ta faɗa itama. Cikin girgiza kai yace, “Ai bama zan bari ku dawo ɗin ba. Daga yau ba zaku sake zuwa ba sai ranar suna.” Zasu fara magiya ya ce, “Okay nace Mammah tai zamanta kada ta dawo goben kenan?”. Ai tuni suka saki batun dawowa gidan suka fara murna jin Mammah zata dawo. Abin zai birgeka har su Auntys ɗin farin ciki suke yi. Shi dai Imran yay ma Baby addu'a sosai ya ɗan zauna suka taɓa hira sannan ya miƙe zai tafi. Dole Aunty Hafsat ta miƙe suka wuce tare. Su kuwa sai anyi sallar magriba sannan koma isha'i.... >>>><<<<★★>>>><<<< ★DUBAI★ Cikin zafin rai take magana kuma da harshen turanci. Shi ko yayi sabale yana kallonta dan komai tayi birgeshi take. Shi kaɗai yasan irin wutar masifar sha'awarta da yake ji tsahon shekaru. Ya kuma kasa binta ta ƙarfi batare da yasan dalili ba. Bayan kuma hakan abu ne mai sauƙi a garesa duk da kuwa yasan tana da aure. Yasan inda wata ce ba ita ba yanda yake narkama uwarta kuɗi duk da hakan ba komai bane a garesa da tuni ya mata fata-fata ta yanda ko rayuwarta sai ya ce ga yanda zatayi sannan zata gudanar da ita. Yanzu haka yana ƙasar Garmany ne harka business ɗinsa Hajiya Hasiba ta tura masa saƙon kudirin Nabeeha, yana gani hankalinsa ya tashi, a take ya kira duk wani Companyn sauka da tashin jirage yasa aka rufe damar Nabeeha na barin ƙasar. Amma duk da haka hankalinsa yaƙi kwanciya a daren ya baro ya dawo dubai ɗin. Kai tsaye gidan nasu yayo, cikin sa'a kuma ya sami Nabeeha a falo zaune ta haɗa kai da gwiwa tana kuka. Zama yay kusa da ita da kai hannu zai taɓata ta zabura, shine take zazzaga masa ruwan masifa data sakashi zuba mata ido kawai yana kallonta... Su Ismat dake laɓe farin ciki ya kamata, dan itama wlhy ta tsani guy ɗin nan, dan bata da wani burin daya wuce Nabeeha ta koma ɗakin aurenta. Ta haka ne kawai itama zata samu cikar nata burin na mallakar Ja'afar. Cike da munafunci Amima ta dannama Hajiya Hasiba kira da mahaifiyarsu data shigo gari tun cikin satin daya gabata. Aiko cikin mintinan ƙalilan suka iso dan duk suna kusa da gida ne dama. Wata tsawa Hajiya Hasiba ta dakama Nabeeha. Cikin zafin rai ta ɗaga hannu zata mareta caraf Adeel ya riƙe hannun. Cike da gadara ya ce, “Karma ki fara dan ina ganin mutuncinki na haihuwarta da kikayi, amma da a maimakon riƙe hannun nan naki sai dai ki jisa a ƙasa yana lilo”. Maimakon jin zafin abinda yay mata murmushi Hajiya Hasiba tayi daga ita har ƙanwarta Mamawo. Cike da girmamawa suka shiga faɗin, “ALLAH ya huci zuciyar babba ɗan manya jinin alkairi. Nayi kuskure ayi haƙuri raina ne ya ɓaci. Taya zata zauna tana gaya maka irin wannan shirmen..” “Karki damu ta isa ne ai, girmanta ne. Ni zan koma kawai, amma zan dawo anjima anan zanyi dinner”. “An gama ranka ya daɗe”. Hajiya Hasiba ta faɗa cike da girmamawa. Yayinda Mamawo ke wani shegen murmushi tana binsa da wani kallo zuciyarta cike da abubuwa. Amma a zahiri baka isa karantar abinda ke ranta ba dan cikakkiyar ƴar bariki ce data iya takunta. Yana ficewa suka koma yima Nabeeha faɗa da nuna mata karfa ta dawo tana dana sani da wannan damar da ALLAH ya bata. Wai miye akai akayi wani Haysam can da bata da tabbacin yana ma raye ko an jima da kashe shi ne. Kuka ta saka musu cike da bori da rashin kunya tabar wajen. Dole sukai shiru bayan duk sun ja tsaki. Bayanta itama Ismat tabi zuciyarta na zafi. Koda ta shiga ɗakin taga Nabeeha ta kwanta tana kuka zaman lallashinta tayi, ganin taƙi yin shiru ta ɗauka wayarta a karo na farko ta danna kiran Jiddah, abinda sai ta jima batayi ba saboda duk haushinta suke ji akan gaskiya da take gaya musu. Received at 2:05 PMReactions: Batai zaton zata ɗaga mata ba ma, amma sai gashi ta ɗaga cikin tsaftatacciyar sallama. Da ɗan rawar murya Ismat ta amsa mata, sai kuma ta fara gaisheta. Ɗan jimmm Jiddah tayi kafin ta amsa tana kallon Abban su dan taje barka gidan Aunty Mimi ne shine ta biyo gidan gaishe su. Kukan da Ismat ɗin ta fashe da shi ne ya saka Jiddah faɗin, “Ismat lafiya kuwa? Ko wani ne ya rasu?”. “Aunty babu wanda ya rasu, kawai abubuwa ne suka mana yawa. Mom ta takura dole sai Aunty Nabeeha ta kashe aurenta ta auri wannan mayen mutumin. Jiya mukai shirin gudowa kawai ta sace passport ɗinmu ta ɓoye. Yau kuma sai gashi yazo. Aunty ki taimakemu ki sanar da Abba yazo ya tafi damu. Wlhy gida muke son dawowa, aunty Nabeeha na son komawa gidan mijinta”. Jiddah dake jin jikinta ma na rawa ta ɗan saci kallon Abbansu. Ai ko yayi kicin-kicin da fuska yama maida hankalinsa a television inda ake hira da ɗan takarar shugaban ƙasa ƙarƙashin jam'iyar SGP, wato tsohon janar ɗin soja kuma ɗan majalisan tarayya mai ci Janar Yusuf Shu'aibu Tafida. Yawu masu kauri ta haɗe, cikin damuwa ta maida kallonta ga Hajiya Zuwaira da suke kira Ummu a gidan. Idan ka cire Nabeeha da Ismat da har yanzu basa ko gaisheta. Kai Ummu ɗin ta girgiza mata alamar ta kwantar da hankalinta, dan taji komai itama kasancewar hansfree ta saka wayar. Cikin dauriya Jiddah ta ce, “Wannan shi nake nuna muku tun farko amma kuka kasa ganewa Ismat daga ke har Aunty Nabeeha. Yanzu dan ALLAH yaushe rabonku da kiran wani a cikinmu har Abban, aƙalla shekara uku kenan fa. Ni kuma kun saka ni a black list kona nemeku bata shiga harta WhatsApp. Ni yanzu a wannan gaɓar mizan iya yi, wane tabbaci ne dani akan baku biye ma Momy ɗin ba akan ƙudirinta.....” “Wlhy aunty bamu taɓa aikata wani abu saɓanin abinda kike tunani ba mu kammu balle Aunty Nabeeha”. Duk da Jiddah bata da tabbaci sai da ta sauke ajiyar zuciya mai nauyi, duk da tasan wacece mahaifiyarsu akan son duniya babu abinda bazata aikata ba. Itafa ko uwarmi zasuyi suyi ba ruwanta tunma suna ƙananunsu indai kuɗi zai shigo fine. Hawayen da suka cika mata ido ta haɗiye, ta ce. “Shike nan Ismat ki bani zuwa gobe, yanzu haka ma bana gida naje barkar Aunty Mimi ne data haihu. Amma zan yi magana da Abban”. “To aunty dan ALLAH ki taimaka mana, ke kaɗai ce hope ɗinmu a yanzu wlhy”. “Karki damu in sha ALLAH duk yanda muke zan taɓoki, ni dai fatana ku cigaba da riƙe mutuncinku kada ku biyema Mom”. “In sha ALLAHU Aunty ki mana addu'a”. “Ita nake muku kullum”. Daga haka ta sauke wayar. Tun kafin ma tai magana Uncle Nasiru ya dakatar da ita da faɗin, “Tashi ki wuce gida dare yayi? ALLAH ya bamu alheri”. Yanzu kam sosai idonta ya tara hawayen, ta waiwaya tana kallon Ummu. Kai ta jinjina mata alamar taje, tabar komai a hannunta kawai. Sai kawai ta miƙe tai musu sallama ta fita. Dama ita ta tuƙo kanta. Aiko tana shiga motar ta kife kanta a sitiyari kawai ya fashe da kuka. Ta jima tana kuka har sai da maigadi yazo yana mata knocking glass sannan ta haƙura ta share hawayenta taima motar key...... <%>°<%>°<%> PRISON Wani zuba masa kaifafan idanunsa yay a hankali, tare da sakin wani murmushi mai zafi da izza, mai tabbatar da cikakken izgili da raini fiye da nashi. Dan a ƙarshe da wani salo irin na maida mutum banza sakarai Dada ya taɓe baki. Sannan cikin son tunzurawa ya ɗan karkatar da kansa, fuskar sa ta cika da izza mai nutsuwa. Like yana magana da wani shasha can ya furta, “Tofa! kaga fa kana ƙoƙarin bani mamaki.” Ya yi murmushi mai ɗan kaifi, ba na farin ciki ba, na jarumin da ya saba da iya riƙe nauyin abu a zuciya da ƙwaƙwalwa batare daya bari abokin gaba ya fahimci lagonsa ba. Cikin halin ko in kula ya cigaba da da ɗin, “Ka zo nan kana min barazana da dorinar ƙarya, ka ce ku ne ƙasa, ku ne haske, ku ne gwamnati. Amma duk da wannan ƙarfin ikon naku kuma kuka zaɓi ɓoye fuska kamar masu tsoron haske a gaban ZAKIN dake ɓoye cikin keji?. Gaskiya ban yarda da wannan ƙarfin ikon naku mai kama dana ƴan wasan kwaikwayo ba, ya kamata ku koma ku canja shiri.” Received at 2:05 PMReactions: Ya ɗan sake matsawa gaban tebirin sosai yana sassauta murya kamar mai son yin raɗa idanunsa na sake shiga cikin na baƙon, sai dai muryar tasa ta cika da nauyin, da ƙarfi irin na masu izzar ƙarfin zuciya da jarumtar ƙwarai dake jinsu ko a ɗaure su ba masu risinawa wawaye bane. “Ɗan aike!. Ka manta da abu ɗaya.” Shiru ya mamaye ɗakin. Baƙon ya tsaya tamkar an dasa shi a wajen yana kallon Zak-Shadow da jin ƙaguwar son barin wajen dan wani irin firgitashi al'amarinsa keyi, dauriya kawai yake da dannewa saboda sanin akwai camara a jikinsa dake ɗaukar komai. Kai tsaye kuma duk abinda suke tattaunawa ƴan ƙungiya ma na kallonsu........✍️ Received at 2:05 PM[01-16, 11:37] +234 703 449 6321: KIƊA A RUWA 2 21 ........Tunaninsa ya katse sakamakon cigaban kalaman Zak-Shadow masu zafi da sanya zuciya raɗaɗi. “Idan kaje ka sanar da iyayen gidanka saƙo daga ni Haysam Abdul-rasheed Shehu. Ku na mallakar gwamnati, amma ba kwa mallakar ƘASA. Ku na mallakar masu muƙami, amma ba kwa mallakar mutanen da suke amsa sunan KASAR. Ka sanar musu. Idan suna tunanin zasu sarrafa ni kamar karnukan su… to su sake tunani tun kafin lokaci ya ƙure musu. Ka faɗa musu. Wannan ba ƙarshen wasan ba bane, farkon rugujewar su ne, domin kuwa yanzu ne za'a FARA WASA na GASKIYA. Ka faɗa musu. Wanda yake da cikakken iko ba ya zuwa ya gaya wa wanda yake tsoro barazana. Domin wannan zuwan naku tabbatar min yay da kun MATSORATA ne, kuma ni abin tsoronku ne. Na ji ƙamshin wannan tsoron naku tun shigowarka nan. Ka faɗa musu. Idan kun kasance da ikon da kuke ikirari… ku kasheni kawai zai fi muku sauƙi da samun cikar burin ku cikin salama” ya ɗan yi dariyar da ta sake tsokano zuciyar bako. Batare da bashi damar cewa komai ba ya cigaba da faɗin, “Ka faɗa musu. In har kukai sakacin ƙin kasheni da ɗaukar zantukana cika baki, to ku shirya… ku shirya wasan da muka fara ba lissafin saƙar zaren ginin gidan GIZO-GIZO ba. Ka faɗa musu. Shi wannan filin da suke cika bakin samarwa domin ƙwallon ƙafa, da jinin da zasu jiƙa ƙasar domin ta tausasa. Ni ne zan samar da filin WASAN, sannan na jiƙa ƙasar da jinin jikinku. A maimakon buga wasan ƙwallo na ɗaura muku sarƙar mata a ƙafafuwa ku zagaye filin da takun RAWAR ƘOROSO. Ka faɗa musu. Ni nake tsara gangar da masu kiɗanta, kuma tabbas in sha ALLAHU sune zasu taka wannan rawar fa. Ka tafi ka faɗa musu. Na gane kun TSORATA. Sannan wannan SAƘON daka kawo zai zama kuskurenku na farko. Na biyun zai biyo bayan fitowata daga nan. Ka faɗa musu. Idan har iyayensu sun haifesu da alfaharin igiyar aure, kamar yanda ni Haysam Abdul-rasheed Shehu Kobi A'isha da Abdul-rasheed suka haifeni da wannan alfaharin ku rubuta kalamaina ku ajiye da yaƙini a saman dutse. Sannan ku shirya.” Ya turo kujerar ya tashi a hankali yana sakin murmurshin ƙasaita tamkar sarki ya miƙe daga gadon mulkinsa. Ya zubama agogon hannunsa idanu na sakanni tare da sake sakin murmushi mai ma'anoni da yawa sannan ya fara takun dake nuna alamar barin wajen. Da sauri shima baƙon ya kalla agogon nashi mai ɗauke da camara saboda kallon da Zak-Shadow yay ma agogon ya tabbatar ɗayan biyu ne, ko dai ya fahimci camara ɗin ce ko ya tsargu.... Dada da yay takun da bai gaza biyar ba ya tsaya cak, tare da juyowa a hankali, idanunsa suka sauka a kan mutumin. Fuska ta bogi, amma mugunta ta gaskiya.... Murmushi ya sake saki da ɗan taɓe baki. Cikin salon isar da saƙon ƙarshe a inda yake da tabbacin masu aiken na kallonsa yanda ya dace domin idanunsa kam a kan agogon mutumin ya furta, “Ni bana kare gwamnati. Bana kare hukumar soji. Bana kare kujerun ƴan mulkin mallaka. Amma ku sani. Na kare ƙasa. Na kare mutanen ƙasa. Na kare gaskiya duk da ƙarfin ikon UBANGIJI mai IZZA da cikar mulki na gaskiya. Wannan kuma… Shine abinda kuke tsoro. Zan ƙara tabbar muku, idan har kuka bar Haysam Abdul-rasheed Shehu a raye, zai cigaba da tabbatar muku wannan tsoron a cikin ZUKATA. Bance zan iya komai ba, amma bazan taɓa raina kaina a gaban ALADU irin ku ba”. Ya ɗan yi shiru yana murmurshi mai ciwo, dan kowace kalma yana fitar da ita ne daga zuciyarsa kamar takobi mai kaifin gayawa jini ya wuce. Baƙo da zuciyarsa ke dukan uku-uku cike da ƙarfin hali ya ɗan taɓe baki, numfashinsa dake fita da rawa ya fisgo da ƙyar dan neman ƙwace masa yake. A karo na farko ya ji wani abu ya motsa masa a ƙirji, ba tsoro bane kawai, ba kuma bakin ciki bane kawai. Bayyanan nen rauni ne dake tuna masa, shima fa ɗan ƙasa ne tamkar Zak-Shadow, yana da dangi a ciki ba iyalai kawai ba, yana da ƙarfin ikon kiranta tushe ba son tara dukiya da ƙarfin ikon son mulki kawai ba.... Dada daya gama fahimtar raunin nasa dake son bayyana ya juya zai fita abinsa yana murmurshi, sai kuma ya sake tsayawa tare da juyowa a lokaci guda. Da tabbatar wa ya ce, “Ya kamata na sake jaddada muku domin fita hakki. Kar ku barni a nan domin in gani daga shirin shirin ku. Idan kukai wannan sakacin zan zauna in rubuta yadda zan rushe ku daga cikin ɗakin nan da wawancin ku ke sakaku kallonsa keji”. Ya kammala da murya mai sanyi, amma mai ɗauke da tabbataccen iƙirari. “Kuna da duhu. Ni kuma ina da hasken da yake huda duhun nan naku. Saƙo na ƙarshe, duk wanda ya sake zuwa inda nake da saƙon ku, zan bashi amsar da zai maido muku. Sai dai GAWARSA ce zata dawo da amsar da gangar jikinsa ba BABU RUHI....” Ya saki murmushi tare da salute da yatsa ɗaya kacal sannan ya juya abinsa cikin takun nan nasa da wanda basu fahimcesa ba ke kallon na izgili da izza. Ƙofar ya buɗe ya fita ba tare da ko waiwaye ba yabar baƙo da rawar zuciya da jiƙewar gumi, ga shi ya gagara koda motsi a wajen tamkar wanda gangar jikinsa ta mutu ta barshi da fitar numfashi kawai........ <%><%><%><%> Cike da nutsuwa take haɗa masa abincin karin a gabansa, duk da kuwa tana daga tsaye ne shi a zaune kan ɗaya daga kujerun daning ɗin. Ya zuba mata idanunsa na girma fuskarsa da murmurshi. Sai da ta kammala zata matsa ya riƙo hannunta. Kallonsa tayi itama a karo na farko, sai dai fuskarta ita sam babu walwala alamar akwai abinda ke damunta ko ranta a ɓace yake. “Juwairiyya mike damunki ne wai?”. Yanda yay maganar cikin taushin murya yana sake tsatstsareta da idanu ya sata sunkiyar da kanta. Sai dai batace komai ba. Numfashi ya ja ya fesar tare da sake matsa hannunta cikin nashi, ya buɗe baki zai magana kenan takun fitowar wani daga cikin yaran ya sashi yin shiru yana sakar mata hannun. Itama matsawa tai kaɗan dan mai fitowar har ya bayyana. Ba kowa bane face Abdul-rasheed da suke kira Imam saboda sunan aboki, amini kuma mahaifi gasu Dada da yaci. Imam shine babban ɗanta a gidan, sa'anni suke shi da Mu'azz koma muce ya girmesa da kusan 2years. Yarone nutsatstse yana tsananin kama da Uncle Nasiru, akwai mai bi masa Halimatus'sa'adiyya. Sai Bintu sa'ar su Nimrah, itama dai ƙawarsu ce dan ƙiriniyarsu ɗaya da ita, idan suka haɗu sam basa jin bari musamman idan an samu hutun makaranta sukan haɗu anan ko gidan Mammah ko gidan Daddy Imran. Adam da Sadiq sune ƙananu a gidan, dan Hajiya Zuwairah ta haifesu ne ma kusa-da-kusa sakamakon gwanne data samu, ta haifi Adam da wata uku ta sake samun cikin Sadiq, hakan yasa tsiransu nasu ba yawa. “Abba ina kwana? Ummu Ina kwana?”. Imam ya faɗa yana mai kaiwa duƙe. Hannu Uncle Nasiru ya miƙa masa alamar suyi musabaha yana murmurshi, yayinda Hajiya Zuwairah ta amsa masa da kulawa. Fuskar Imam da murmurshi ya bama Abban hannu kamar yanda yake masa kullum. Dai-dai lokacin Sadiyya da Bintu ke fitowa suma dan ɗakinsu ɗaya. Abba ya ce, “Abdul-Rasheed kaifa abokina ne ba suruki ba”. Murmurshi Imam yayi kamar yanda ya saba a duk sanda Abban nasu ya faɗi haka. Hakama Hajiya Zuwairah na tayashi. Imam na kaiwa zaune a kujera shima su Bintu suka ƙaraso dining ɗin, cikin girmamawa suka gaida Abban sannan Ummu da Yaya Imam. Duk sun amsa musu da kulawa, Ummu ta kalli Sadiyya tana faɗin, “Halimatu taso min su Adam suzo suyi kari, dan yanzu haka ma basu tashi ba balle batun tafiya Tahafiz, ni narasa miyasa kukafi ɗaukar tafiya boko da muhimmanci a rayuwarku fiye da islamiyya”. Sadiyya data zama budurwa sosai tai ƴar dariya da faɗin, “Ummu itama islamiyya muna so ALLAH, baga Yaya Imam nan ba har jami'a fannin Islamic ya zaɓa”. “To ai shi dama yana son karatun addini ba irinku ba. Dan magajin mai sunan nashi ne da Haysam.” Hajiya Zuwairah ta bata amsa. Murmurshi Uncle Nasiru yayi, zuciyarsa na tuno masa amininsa kuma ɗan uwa Abdul-rasheed, tare da jin raunin zuciya na gagara taka kowacce irin rawa akan al'amarin babban ɗa na ƙwarai irin Haysam. Received at 12:46 PMReactions: [01-16, 11:37] +234 703 449 6321: KIƊA A RUWA 2 22 .........“Wlhy Abba zasu aika kada ka amince da daɗin bakinta. Idan ba haka ba nima sai dai a maida ni makarantar su Asma'u ai ƙawaye basu ƙawaye ba”. Caraf Adam yace, “Muma haka Abba”. Dariya kowa ya sanya. Abba ya shafa kan Adam da Sadiq. “Kenan dai na gane a gidan nan kowa yana jealous da Mamana kawai”. “A da alama kam”. Cewar Ummu tana murmushi. Itako Bintu tayi kicin-kicin da fuska alamar jin haushi. Sai da Ummu ta lallasheta sannan ta yarda ta zuba abinci. Daga haka suka nutsu suka fara karyawa babu mai magana. Sai da suka kammala kowa ya miƙe dan zuwa yay shirin Tahafiz har Imam. A lokacin ne Uncle Nasiru ya sake kallon Hajiya Zuwairah dake gyara gurin duk da su Bintu duk sun kwashe kwanikan sun kai kitchen. “Zamu iya magana yanzu?”. Kallonsa ta ɗanyi, sai kuma ta tura baki kama ƴar yarinya. Dariya yayi yana haɗe hannayensa da faɗin, “To ni dai duk ma laifin da nayi ayi haƙuri ai min afuwa. Amma dan ALLAH a sanar min damuwa kada zuciyata ta sake kumbura.” Kanta ta sunkuyar kawai batare da tayi murmushi data saba yi ba a duk sanda yay irin wannan maganar, sai kuma ta ɗan sauke numfashi cike da nutsuwa ta ce, “Abban Jiddah akan maganar jiya da kaƙi sauraren Jiddah akai ne. Bayan kuma ni da kai duk munji abinda Ismat ta faɗa fa. Yanzu dan ALLAH sai ka bari ɓacin rai ya rinjayeka barin yaran nan a cikin tarkon musiba? Kana jin fa abinda ke faruwa; a tunaninka watarana mahaifiyarsu bazata ci galaba akansu ba musamman ma Nabeeha dake ɗauke da igiyoyin aure a kanta! Nasan Nabeeha mai laifi ce a gareka, dan babu izninka babu na mijinta ta koma wata ƙasa da zama bayan ana cikin damuwa da halin da mijinta ke ciki, amma abinda zamu kalla ko tana da laifi wani kaso ne a ciki Hajiya Hasiba nada wani, saboda tana da tasiri ƙwarai da gaske akan al'amarin yarannan idan ka cire Jiddah da ALLAH yay saurin fargarwa...” Cikin ɗacin murya da sauyawar idanun da ɓacewar murmushin kan fuskarsa ya ce, “Ya kike so nayi Juwairiyya? Shin basu ne suka zaɓi irin rayuwar ba shiyyasa suke ciki? Ai su duka ba yara bane har Ismat ɗin da ake ganin batai aure ba, amma suke biyewa gafalar uwarsu da son duniya ta rufema idanu ko”. “Hakane, amma abinda zamu duba har yanzu su yara ne akanmu. Sannan mata ne. Mufa mata a kowace sigar rayuwa a karkacen nan muke tamkar haƙarƙari. Shekaru basa saka mu canja ko ilimi. Sai wanda UBANGIJI yaso ya gane kawai daga cikinmu. Mu godema ALLAH da yarannan basu tasirantu da huɗubarta ba ma har suka fahimta illar al'amarin. Dan wlhy UBANGIJI ne kawai ke riƙe da igiyoyin auren Nabeeha saboda Haysam mutumin kirki ne, in sha ALLAHU ALLAH bazai haɗa masa zafi biyu a lokaci guda ba. Dan ALLAH kayi wani abu kodan Haysam, saboda koba komai da saka hannunka ya auri Nabeeha, sannan yana sonta”. “Hummm Juwairiyya....” “Dan ALLAH karka ce A'a Abban Jiddah”. Tai maganar cikin katse masa hanzari. Ajiyar zuciya ya ɗan sauke kawai. Tare da faɗin, “Shike nan zan duba. Amma ki sani Adeel yaro ne mai dauɗar duniya a hannu, sannan ya fito daga babbar zuri'ar da yake da ƙarfin aji ako ina a duniya musamman ma ƙasashenmu na Afirika. Barowarsu ƙasar nan zai zama babban al'amari. Amma zan gwada wata hanya idan za'a dace.” “ALLAH yasa a dace, dan duk ƙarfinsa bai kai na UBANGIJI ba ai. Darajar auren dake kan Nabeeha ALLAH zai hanashi dukkan nasara. Itama ALLAH ya shiryar da ita ta gane halakar da take neman jefa yarannan da kanta.” “HUmmm”. Kawai Uncle Nasiru yace, itama sai ta saki zancen ta ɗakko na batun zuwa sake duba Aunty Mimi mai haihuwa duk da kuwa randa ta haihu taje. Amma a matsayinta na kamar uwa koda Mammah na nan dama ita ya kamata ta yi abinda uwa zatayin, saboda ita da Mammah suna jin kansu kamar ya da ƙanwa uwa ɗaya uba ɗaya. Kamar yanda Uncle Nasiru ke ɗaukar Mammah ƙanwarsa uwa ɗaya uba ɗayan. Bai hanata ba, shima ya miƙe yana faɗin zai shirya dan yau yana da ganawa da sanata Yusuf Shu'aibu Tafida tsohon janar. Received at 12:46 PMReactions[01-16, 11:37] +234 703 449 6321: ƘIDA A RUWA 2 23 .........A wannan rana ƙarfe sha biyu na rana jirgin su Mammah ya sauka, tare take da Ammar ɗinta sai ƙaninta Tasi'u da Ammar ke kira Uncle. A tsakkiya suka sakata har inda motoci suke. Aiko cikin sa'a sukai arba da tagwaye biyu Yaya Ma'aruff da Ja'afar da suka zo ɗaukarsu da kansu. Sai dai me suna yunƙurowa a tare suka koma suka ƙame kamar gunkinaye idanunsu akan Uncle Tasi'un. Dan duk da suma suna yara sosai ya aikata abinda ya aikata hakan bai sa sun mance wannan fuskar tasa ba. Dan bayan mahaifin Biebah shine mutum na biyu daya bar musu tabo a zuciya na zahiri. Abinda dangin mahaifinsu suka aikata duk a labari suka sanshi, a labarin ma ba komai ba daga bakin Mammah ko Dadansu. Gwaggo Alawiyya ce ta gaya musu komai. Ganin yanda sukai ɗin ya saka Mammah cikin dakewa furta, “Oh bakwa farin ciki da ni na koma kenan ko?”. Jikinsu ne yay sanyi, cikin dauriya da danne zukata suka nufota, batare da ko kallon Uncle ɗin nasu sun sake yi ba suka rungumeta ita da Ammar suka manta da shi. Ammar daya tsargu da abinda ya farun da ƙyar ya iya dannewa yana murmurshi. Haka suka kama Mammah a tsakkiya har mota. Sai da ta shiga suma suka shiga Ammar ya shiga, ganin Uncle Tasi'un bai shigo ba Mammah tace su masa magana ya shigo. Kallonta sukai kamar zasu fasa kuka. Amma kallon da itama tai musu na gargaɗi ya sasu risinar da kawuna Ja'afar ya fita yay masa magana. Sum-sum kamar munafuki ya shiga kusa da ita suka sakata a tsakiya shi da Ammar...... Sun iso gida da yake shiru kasancewar basawan cikinsu duk ana makaranta. Masu aiki ne kawai sai Aunty Shariffa da Aunty Lailah da yay basu je gidan haihuwa ba saboda dawowar Mammah. Hasalima da kansu suka shiga kicin yi mata abincin da suka san tafi so da ƙauna. Masu aiki da suma ke farin ciki da dawowarta na tayasu da ƙananun ayyuka. Daga Aunty Shariffa har Aunty Lailah kowace fama take da ƙaramin ciki, dan cikin ikon ALLAH kamar yanda sukai haihuwar su Abees a tare da tasu Afrah da Ayyan haka wannan cikin ma basu da nisa a samu. Sai dai Aunty Lailah ce ta fara samu kafin Shariffa. Dan haka nata yafi fitowa sosai har ana iya gani. Mu'azz ya fita akan batun karatunsa dan Imam ne yazo har gida suka fita a mashin ɗinsa. Wannan ya ƙara haifar ma da gidan shiru. Motar su Mammah na gama tsayawa Lailah da Shariffa suka fito cike da ɗoki da farin ciki dan Mammah uwa ce a garesu ba uwar miji ba. Itama fuskata ƙawace da murmushi ta fito da taimakon Ammar. A tare ta kamosu jikinta ta rungume tana mai jin farin cikin ganinsu da sanya musu albarka. Yayinda suma suka zame suka zube cike da girmamawa suna mata barka da dawowa. Ta amsa musu da kulawa tana kamasu ta miƙar. Cike da tsokana Ammar ya ce, “Wato kunga Mamanku ni in ma na ɓata a can babu ruwanku ko Auntys?”. Yanda yay maganar yana cika baki da iska har su Ma'aruff dake faman haɗe fuska saboda Uncle Tasi'u Sai da suka dara. Suma cike da tsokana sukace, “Mu mun isa muso kawun yara ya ɓata. Ai sai suyi mana bore suma Yaya Ammar”. “Ato naga ba'a wani ji dani ne sai Mammah kawai”. “To ayi haƙuri, kasan rashin ta ya maida mu kamar marayu a gidan cike muke da ƙaguwar son ganinta. Kaima bari kaga ƴaƴanka su dawo duk kanka zasuyi”. “Ai shiyyasa ma ban damun ba. Dan da kaina zanje na ɗakkosu a schools”. Duk hirar da suke zugawa Uncle Tasi'u na kallonsu ne kawai cikin damuwar kallon banzar da su Ja'afar ke masa a kaikaice. Su ko su Lailah basu lura da shi ba sai daga baya. Kamaninsa da Mammah dake a bayyane ya sakasu kasa jurewa suka bishi da kallon sakanni. Sai kuma suka duƙar da kawuna cikin ƙaulani da rashin tabbaci suka shiga masa barka da zuwa. A karo na farko yaɗan sauke ajiyar zuciya. Dan koba komai girmamawar tasu ta ɗan sakashi jin sanyi a ransa. Ya amsa musu da kulawa shima. Mammah ta katse su da faɗin, “Kumuje ciki kun san fa ni bana jurar tsaiwa”. Received at 4:52 Da to suka amsa mata suna sakata a tsakkiya, dai-dai nan kuma maigadi da sabon driver suka iso wajen cike da girmamawa suka duƙa har ƙasa suna gaida Mammah. Tabbas Mammah zata iya haihuwarsu idan muka musalta da yanayin auren da na ƙarancin shekaru musamman ma itama da akai mata tana ƴar 14. Dan driver dai zai iya zama sa'an Dada, maigadi ko bai wuce sa'an su Yaya Ja'afar ba, idan ma Dada zai girme ma sabon driver ɗin kaɗan ne, sai dai yanayin jin daɗi ba ɗaya ba, duk da a yanzu basu san yaya Dadan yake ba amma ya fishi ƙyawun jiki da ƙuruciyar zahiri. Dan shi wannan ma har furfura ta cika masa gemu duk da dai kansa akwai hula tashi da ƙwaƙwa baƙa data ɓoye gashin kan nasa, sai na iya fuskar zaka shaida zuwa gemu dan yana da saje... “A'a bawan ALLAH tashi-tashi kaji, mun sameku lafiya ko Almu. Ka yi baƙo ne?”. Maigadi ya bata amsa da mata bayanin ba baƙonshi bane su Yaya Ma'aruff ne suka kawo shi. Kafin tace wani abu sabon driver wanda shima a karo na biyu fuskarsa da murmurshi ya amsa mata, kafin ya miƙe yana sake mata barka da dawowa da sannu da jiki. Sannan ya juya yana gaida Uncle Tasi'u da Ammar. Ma'aruff ne ya juyo yana kallon Mammah ya ce, “Sabon driver ne daya maye gurbin Baba Ari. Sunansa Buba kwana uku da tafiyarku ya fara aiki”. Fuskar Mammah da fara'a sosai ta ce, “Masha ALLAH. Sannu da zuwa Malam Buba. ALLAH yasa zamanmu tare ya zama alkairin da zamu shiga aljanna gaba ɗaya. Ina dai fatan babu wani damuwa a zamanka tare da mu ɗin?”. “Amin Hajiya. Amin Amin. Babu wata damuwa sai godiya tsakanina da ku. Dan kuwa kwanakin da nai kawai na shaida alkairin mutanen wannan gida.” “To Alhamdullahi ALLAH yasa mu dace. Bari naje na huta munsha zaman jirgi zuwa anjima ka shigo mu ƙara gaisawa?”. “To to shike nan Hajiya, ALLAH ya huta gajiya nagode sosai.” Fuskar Mammah da murmushi ta amsa da amin Kafin su Shariffa su kamata har zuwa ciki. Shi dai Uncle Tasi'u na biye da su sum-sum kamar munafuki, sai dai harga ALLAH yayi matuƙar girgiza da ganin irin wannan katafaren gida mai kama da wani ƙaramin estate wai duk mallakin Adda A'isha ne da zuri'arta. Addarsa fa dake wujiga-wijiga akan marayun ƴaƴanta dana gayyar soɗi na kishiya data kama ta riƙe ita mai son miji. Addar nan tasa dai daya damfara gida ya gudu ya batta da sanin bata ga tsuntsu bata ga tarko a lokacin, amma a yanzu sai gasu a wannan ƙosashen gidan a babban birnin tarayyar ƙasa da dukkan alamu suka nuna nasu ne, kai shifa tun a motar dasu Ja'afar ɗin suka ɗakkosu dama zuciyarsa ke bugawa, yanzu kuma da suka shigo gidan ma sai yaga motocin da sukafi wadda suke ciki, sannan ba ɗaya ba a ƙalla motoci sun kai bakwai a gidan harda wadda suka dawo ta takwas. Bai ji zuciyarsa na tsitstsinkewa ba sai da suka shiga cikin katafaren sashen Mammah ita ɗaya, dan dama sashenta dana Dada sunfi kowanne girma a gidan. Kafin kace mi kuma ƴan aiki har uku sun zagayeta suma da tasu gaisuwar girma. Ga waɗan nan tsala-tsalan matan daya fahimci matan su Ja'afar ne sai rawar jiki suke akanta kamar wata uwarsu mahaifiya... .....★DUBAI★..... “Inaga a wannan gaɓar zan saka a kashe mijin nata, dan hakan ne kawai zai saka ta yarda ta saduda ta mallaka min kanta”. A wani irin firgice Hajiya Hasiba ta ɗago tana kallon Adeel mai maganar. Mamawo kuwa abincin da suke ci ne ya nema ƙwareta. Sai da ta ɗauki ruwa tasha da sauri. Shi ko ko'a jikinsa, dan tamkar ma bai ga halin da suke ciki ba ya cigaba da maganarsa. “A karo na farko ina son sanin wanene shi mijin nata? Miya taka a ƙasar taku? Ɗan wace zuri'a ce? Miye ƙarfin ikon sa?”. Su duka biyun rasa mai bashi amsa akayi, dan dama daga su sai shi ne a dining room ɗin. Su Ismat sunbi Nabeeha sun fice a gidan tun da sukaji zancen zuwansa. Ɗan dukan table ɗin yayi ta yanda suka dawo hayyacinsu firgigit. Da ƴar tsawa da raini da wulaƙanci ya ce, “Ko kuma kuna bin bayan wulaƙanta ni da take ne....?” Received at “A'a wlhy bama bin bayanta. Da muna da iko da zuciyarta ma da tuni kun jima da zama ma'aurata maybe ma kun haihu. Mijinta ba kowa bane, ba ɗan kowa ba, baya da komai, baya taƙama da komai. Kawai soja ne a ƙasar mu, kamar yanda muka sanar maka tun farko kuma yana prison yanzu haka, shekaru ashirin da biyar kuma aka yanke masa a can”. “What! Shine kuma take tunanin zaman jiransa?”. “Shirmenta ne kawai Prince, amma tun kan ya shiga prison ma ita ta bar masa gidan sakamakon auren yarinya ƴar shekara 7 da yayi saboda ya ɗakota a wajen yaƙi. Daga ƙarshe ma mukaji ashe shine ya kashe mata iyaye dan ya aureta, da alama wani laƙanin asirin aka bashi dan dama yanda yake juya sojojin da wani gadararsa har manyan suna tsoronsa kai ka san ba haka kawai bane, dole akwai aikin asiri a ciki”. “Woow naji daɗin wannan labarin ƙwari da gaske. Yanzu ita yarinyar tana ina ne?”. “Tana a gidansu tare da ahalinsa. Sai dai a yanzu takai kusan 15years da wasu watanni”. Komai bai sake cewa ba ya miƙe kawai, da kallo suka bishi yana tafiya cike da ƙasaita da gadara, sai da yaje gab da fita a dinning room ɗin sannan ya juyo yana kallonsu. “Zamuje ƙasarku tare da ɗaya a cikinku”. Daga haka ya fice abinsa batare da jiran amsarsu ba.........✍️ Received at [01-16, 11:37] +234 703 449 6321: KIƊA A RUWA 2 24 ..........Shiru sukai kowa ya gagara iya cewa komai. Sai zuwa can Mamawo ta ja numfashi mai ƙarfi ta furzar. Sai kuma ta ajiye spoon ɗin hannunta ta rabga tagumi da hannu biyu. “Anya Aunty mutumin nan bada wata manufa yake son Nabeeha ba?. Wlhy nikam al'amarin nan fa ya fara bani tsoro gaskiya. Duk matan ƙasar nan ko a cikin nan Dubai irin sa, da masu shigowa baƙi kullum, dana ƙasashen da yake yawo ace ya rasa matar aure sai Nabeeha da aka jima da sanar masa tana da miji. Abin mamaki duk cin kashin da take masa bai taɓa nuna koda damuwa a fuska ba balle zuciyarsa. Kai wannan batu yana buƙatar dubawa fa. Kalla gidan nan daya mallaka miki halak mallak, ga motar hawa, mu dukanmu yasa akai mana katin zama ƴan ƙasa. Yanda suke da ƴanci a ƙasar nan haka fa muma muke da ƴancin shiga duk inda muke so a lokacin da muke so..” “Ni kaina a wannan gaɓar na fara tsorata Mamawo. Balle ma maganar kashe Haysam da yayi, bawai bana son ya kashe san ba. Nasan wannan kuma abu ne mai sauƙi a wajensa aikata hakan. Babbar damuwar wataran Nabeeha tasan yanda komai ya faru wlhy bazata rufa mana asiri ba. Dan tsaff zata ce damu aka haɗa kai akayi. Shi yana da kuɗi da mulkin da zai cire kansa, muko mune a ruwa..” “Tabbas zancenki na kan hanya Aunty, sai dai ai zamu iya roƙonsa karya sanar mata, sannan zuwan da zai yi ma duk yanda zamuyi kawai muyi kada ta sani. Dan na tabbatar ya samu Nabeeha duk abinda muke so a duniyar nan zamu sameshi a wajensa, ni dai kawai babbar damuwa ta mu fara sanin wai minene ma manufarsa akan son nata”. “To ta yaya zamu sani kuwa Mamawo? Tunda ba zuciyar tasa zamu tsaga mu duba ba”. “Ai bata wannan ake gane sirrin zuciya ba Aunty, shiryawa zakiyi wuff muje India wajen mai mun aiki, koma minene shirinsa sai ya sanar mana shi”. Shiru Hajiya Hasiba ta kasa magana. Bawai bata bin bokaye bane, sai dai mafi yawa irin wannan leƙe-leƙen bata yinsu a karan kanta first lady ce ke aikenta, kuma tunda suka sauka a mulki ta ɗan rage yi sai na kan kasuwanci da takan je mata, wani lokacin kuma suje tare..... “Aunty kinyi shiru?”. “Ba shiru nayi ba Mamawo, ina auna yanda tafiyar tamu zata kasance ne, balle kinji shi yace zai tafi da wata a cikinmu. Kinga bamu da tabbacin yaushe ne ko?”. “Haba aunty mu sai kace ba mata ba. Zaki iya bagarar da shi akan tafiyar gaggawa ta taso miki wani business ɗinki haka. Kinga sai muyi mu gama da wuri mu dawo. Dan haka ya kamata ma ace cikin watan nan mu tafi”. “To bari muga zanyi tunani”. Daga haka ta miƙe tabar haɗaɗɗen dinning room ɗin da aka cika kayan abincin alatu duk saboda Adeel. Sai gashi ko cikakken lauma uku baiyi ba ya tashi ya barsu da kayansu..... <%><<<%>>><%> Mintuna talatin da isowar Mammah da Ammar su Aunty Ummi suka shigo gidan ita da Aunty Mommy. Cikin matuƙar farin ciki suka rungume Mammah dan yanayin ta kaɗai ya tabbatar musu da lafiya ta ƙara samuwa Alhamdullah. Suma dai hankalinsu bai kai ga Uncle Tasi'un ba sai da suka gama gaishe-gaishen su. Turus sukayi suna kallonsa. Ba kallon sani ko tuna waye shi ba. Kallon mamakin kamaninsa da Mammansu kawai. Dan suma sanda wancan abin ya faru basu da wayon tuna komai gara ma Ma'aruff da Ja'afar ɗin. To balle ma Mimi ƴar ƙarshe ita da Ammar da lokacin basu wuce shekaru shuda ba. Biebah kuwa na jaririyar wata baifi biyu ba. Maida kallonsu sukai ga Mammah, kafin ma suce wani abu ta basu amsa da, “Kawunku ne”. “Kawunmu Mammah? Na ina to? Mudai a sananinmu ƙannenki duk sun rasu, gashi kuma yana kama da ke”. Sai da ta ɗan girgiza kanta da murmurshi kawai sannan ta ce, “A'a Bashir ne dama ALLAH yay ma rasuwa, Tasi'u kam ƙaddara ce ta nisanta mu”. A take murmushin fuskokinsu ya ƙarasa ɓacewa. Dan duk da bata taɓa basu labarin abinda Uncle Tasi'un ya aikata mata ba duniya ta jima da sanar musu. Koma suce cikin danginta. A taƙaice sukace, “ALLAH sarki”. Tare da gaisheshi sama-sama suka bar wajen. Cikin sake raunanuwar zuciya Uncle Tasi'u ya bisu da kallo. Received at 4:52Mammah da duk take jin babu daɗi da yanayin tarbar da ɗan uwan nata ke samu wajen ƴaƴanta cikin sanyin murya ta ce, “Sai kayi haƙuri da abinda zaka gani a wajensu. ALLAH ne shaida ban taɓa sanar musu koda kuskuren dangin mahaifinsu ba balle naka a gareni, sai dai yau da gobe ta wuce wasa duniya da dangin sun gama sanar musu batare dana sani ba. Amma ka bani lokaci ƙanƙani, in sha ALLAHU zan zauna da su ni da Yaya Nasiru zasu fahimta”. Murmurshin ƙarfin hali yayi cikin girgiza kai. “Ba komai Adda, kuma ki sani ni banga laifinsu ba sam. Kawai ina jin tsoron isowar yaran nan da kullum zancen su danginsu danginsu kuma su fuskanci abinda bashi nake fata ba daga dangin. Nine nai laifi basu ba, dan haka dan ALLAH ko sunzo suyi haƙuru su su amshesu koda ni bazasu ashe ni ba”. “Kaima zasu amshe kan in sha ALLAHU. Kadai bani lokacin. Bismilah muci abinci sai ka samu kaje ka watsa ruwa lokacin Azhar na gabatowa. Yanzu kuma gidan zai sake rikicewa dan masu shi na gab da dawowa daga makaranta”. Murmurshi kawai yayi. Ya gyara zama ya fara cin abincin da aka shirya musu a tsakkiyar falon.... ★★★ “Tab ɗi, wai yaya mi hakan ke nufi? Miya kawo wannan mutumin rayuwarmu a wannan gaɓar? A ina ma su Mammah suka samo shi wai shin?”. Ya ƙare maganar tana kallon Ammar. Ammar cikin sake ɓata fuska ya ce, “Aunty acan muka haɗu da shi cikin asibiti fa. Ni kaina nayi mamaki da Mammah ta bashi damar wai ya biyomu, nazata kawai zata barshi ya koma inda ya fito ne”. Hawaye Aunty Momy ta share, muryarta na rawa ta ce, “Sun manta damu a lokacin da muke buƙatar tainakonsu da ƙarfinsu. A yanzu zasu fara dawowa rayuwarmu kenan a lokacin da ƙarfinsu ya ƙare mu mukai ƙarfin. Ni tsorona ma kada ya sake zuwa yaye dukiyar tamu ne ya gudu”. “Shi ɗin banza”. Cewar Ja'afar a hasale. Ya cigaba da faɗin, “Ai ko a wancan karon dan Dada baya nan ne ya samu nasara, kuma yana da hakki a wancan amma a wannan fa. Ko a yanzu da babu Dada akwai halifofinsa a kusa. Idan da rabon yazo yayi ta ransa ne bismilah”. Cikin furzar da iska Ma'aruff ya ce, “Wlhy ni nama rasa tacewa sam. Amma al'amarin ɗan adam bai taɓa bani ƙarshen mamaki ba irin yau. Wai dama Uncle Tasi'u har yana da ƙarfin zuciyar iya sake tunkarar Mammah?”. “Ai baida kunya Yaya Ma'aruff gashi kuwa yayi ka gani. Wlhy ina matuƙar jin kewar Dada. Ya ALLAH ka saka mana ka tarwatsa farin cikin duk wani azzalumi dake da hannu a kama mana shi. Wlhy wani cin kashin ma da yana nan da bazasu kwatanta mana shi ba. Dan na tabbatar duk tsawon shekarun can saboda shakkarsa yasa ko ƴan Bauchi kasa sake tunkarar inda muke. An kama shi dan kar su zo mu nema taimakon sun suka sake ja baya damu. Yanzu kuwa tunda sunga ALLAH ya rufa mana asiri zasu fara kawo kansu...” “Ai ko zasu fuskanci wulaƙanci da tozarci a garemu. Dan mu mun jima da sallama dangi a duniyar mu. Mune dangin kammu mahaifiyarmu da Dada sun ishemu uwa uba a duniya. Azzalumai kawai masu matacciyar zuciyar watsar da marayu”. Ammar ne ke maganar yana kuka. Rungumeshi Ja'afar yayi yana shafa bayansa. Haka ma Aunty Momy hawaye take ta sharcewa ita da aunty Ummi. Kasancewar a sashen Yaya Ja'afar suke zaune sai suka ƙi komawa sashen Mammah har sai da yara suka dawo school. Basa son su fahimci komai dan haka suka dawo sashen Mammah ɗin. Inda suka sameta zagaye da yaran cike da farin ciki kowa ji yake kamar ya koma cikinta. Ita ko bakinta ya kasa rufuwa. Abinci ma ita ta dinga basu abaki tun daga kan Nimrah, Ruƙayya, Abees, Aheel, Afrah da Ayyan ƙarami. A haka shima Mu'azz da Imam suka shigo gidan suka samesu. Suma daɗi ya kamasu da ganin Mammah ta dawo. Ai tuni suma sunyi zaman dirshan suna amsar abincin. Wannan farin cikin ya saka su Aunty Ummi mantawa da damuwarsu. Dan Mammah na kammala bama yaran abinci suka dawo wajen Uncle Ammar shima kowa na tambayar tsarabarsa. Musamman Nimrah da Ruky da suka bada sakwanni na musamman...... <•><•><•><•><•> Received at Kusan lokaci ɗaya Uncle Nasiru da Daddy Imran suka shigo gidan. Dan dukansu daga wajen aiki suke. Sabon Driver dake zaune tare da maigadi ya bisu da kallo su duka. Dan yau kwanakinsa shida a gidan bai taɓa ganin Uncle Nasirun na, sai Imran sau 1 shima. To Daddy Imran ɗin kuma yayi ƴar tafiya bayan wucewar Mammah da yazo sau ɗayan daya gansa, kwanansa huɗu ya dawo. A randa ya dawo yazo gidan lokacin shi kuma yaje ɗakko yara daga Islamiyya. Motarsa na fita shi kuma ya dawo da su. Tun ranar kuma bai sake zuwan ba sai yau. Uncle Nasiru kuwa dama tunda Mammah tai tafiya bai leƙo gidan ba saboda ayyuka sun masa yawa, ya kuma san yaran duk ba zama suke ba sai matan su Ja'afar kawai. Suna tsaka da gaisawa Maigadi ya gama rufe gate ya nufesu, dole shima driver ya bishi suka iso inda suke. Rissinawa sukai suna gaishesu duk da kusan sa'an Imran yake shi sabon driver, koma ya iya girmarsa kaɗan duk da shi Imran akwai jin daɗin rayuwa da kulawa da lafiyar jiki irin ta soja a tattare da shi. Uncle Nasiru yana tsokanar su. Shi ko Imran sai ya ɗan zuba ma sabon driver idanu. Har sai da Uncle Nasiru ya ce, “Imrana yaya dai? Ko ka san shi ne?”. Cikin ɗan murmushi Imran ya girgiza kai da faɗin, “A'a Uncle. Kawai na tafi wani tunanin ne daban”. Bai jira amsawar Uncle Nasiru ba ya juya ga drivern ya amsa masa gaisuwarsa. Daga haka suka bar wajen driver na binsu da ido. A zuciyarsa kam dake bugawa ayyanawa yake (lallai akwai matsala. Shegen nan ko bai gane ni ba ya tsargu da ni. Lallai dole na canja takuna kenan. Dan banzo nan dan na tafi batare da na kammala abinda ya kawoni ba) a zahiri kam miƙewa yay ya koma gate ya zauna a kujera. Sai kuma ya zaro wayarsa ƙaramar nokia ya shiga danne-danne kafin ya kai kunnensa.....[01-16, 11:37] +234 703 449 6321: KIƊA A RUWA 2 25 ..........★A falo kam daga Imran har Uncle Nasiru sunji matuƙar daɗin ganin yanda jikin Mammah ya ƙara ƙyau. Da alama ta samu maganin da yafi wanda take samu anan gida. Dan wannan ne karon farko da suka fita Egypt ɗin dama. Kasancewar su Nimrah duk sun wuce islamiyya da ƙyar gidan shiru, dan ca sukai bazasu ba yau suna murnar dawowar Mammah. Sai da Yaya Ma'aruff ya fatattakesu sannan kowa ya wuce baki a sama. Sai Biebah kawai itama bata jima da dawowa daga school ba. Mu'azz yabi Imam gida. Mammah ta kalla Biebah dake laƙai-laƙai ɗin cin abinci saboda bata jin daɗi yau da ciwon kai ta dawo makaranta ganin Mammah ɗin ne ma ya ɗan watsakkar da ita. Sai dai ganin baƙon dake gidan ya tsaya mata a zuciya kamar sauran ƴan uwanta. Dan yanzu haka ma Aunty Momy da Aunty Ummi da Ammar na ɗakinta suna sake tattaunawa. “Biebah tashi kira Uncle ɗin ku”. Idanu Biebah ta ɗago tana kallon Mammah, sai kuma ta amsa da to cikin sanyi tana tashi. “Kina lafiya kuwa Biebah?”. Cewar Imran. Idanunta na cika da ƙwalla ta ce, “Yaya kaina ke ciwo”. “Ayya Auta stress ne sannu. Jeki dawo kizo kisha magani kije ki ɗan kwanta kafin akkunayen gidan su dawo su hanaki”. Kai ta jinjina masa. Shima Uncle Nasiru yay mata sannu. Nan ma amsawa tai ta wuce aikar Mammah... Babu jimawa ta dawo tace yace gashi nan zuwa. Bata zauna cigaba da cin abincin ba ta ɗauka plate ɗin takai kitchen. Koda ta dawo da ruwa a hannunta ƙoƙarin wucewa tai ɗaki. Dai-dai nan Uncle Tasi'u ya shigo falon da sallama. Duk amsawa sukai suna kallonsa. Sai dai zaram Uncle Nasiru ya miƙe yana kallonsa. Shi ko Imran bai san shi ba a zahiri sai labari a sanda wancan abin ya faru, dan haka babu wani alamun mamaki ko damuwa a tare da shi. Sai ma sannu da zuwa da yake jera masa. Sai dai ya gagara amsawa dan hankalinsa shima gaba ɗaya yana kan Uncle Nasiru ɗin ne. “Tasi'u!”. Uncle Nasiru ya faɗa cikin matsanancin mamaki da al'ajabi. Karo na farko Tasi'u yay ƙasa da kansa, idanunsa na cika da ƙwalla. Fin sakan biyar kafin ya sake ɗagowa tare da takowa inda Uncle Nasiru yake ƙafafunsa nayi kamar suna rawa. Yana zuwa gaban Uncle Nasirun kawai sai ya zube akan gwiyawunsa. Imran ya zaro idanu waje sosai yana miƙewa, dan zuwa yanzu kam ya fahimci lallai akwai matsala, sannan baƙon yana tare da wani babban al'amari, yo dukda ba yaro bane babba da shi ya durƙusama Uncle Nasiru. Mammah ya kalla, ya ga ta duƙar da ƙai itama kamar mai kuka. Sai shima ya girgiza kansa. Muryarsa a raunane ya ce, “Mammah waye shi dan ALLAH? Naga kuna kama ba ɗan uwa bane ba shin?”. Ɗagowa Mammah tayi ta kalla Imran tana ƙoƙarin maida hawayen da suka cika mata idanunta. Fuskarta da ɗan murmushi. Babu wani ko ɗar ta amsama Imran tambayarsa. Dan har cikin ranta kallon Imran take dai-dai da su Haysam. Jinsa take tamkar ɗan data ɗauki cikinsa ta haifa. “Imran Tasi'u ƙanina ne uwa ɗaya uba ɗaya. Baka san shi bane saboda wasu abubuwa da suka faru a baya. Amma sun riga sun wuce na yafe masa. Mun haɗu da shi a asibiti nd kwana huɗu kenan.” Gaba ɗaya Imran sai yaji kamar ma yayi mutuwar tsaye. Ga kukan Uncle Tasi'u daya cika falon. Dan kuwa ya riƙe ƙafafun Uncle Nasiru ne yana raira kuka da kalmomin ban haƙuri kamar wani yaro. Yayin da shi Uncle Nasirun ya gagara sake iya cewa komai yana tsaye kawai shima idanun nasa sun kaɗe jazur. Kukan Uncle Tasi'u ne ya sakko da su Aunty Ummi. Ko muce Biebah taje ta kirasu dan komai dake faruwa tana kallo daga inda take laɓe. Ammar daya gama kaiwa wuya cikin fushi ya ce, “Ni wlhy wannan drama ɗin ta isheni haka nan.” Duk juyawa su Mammah sukai suna kallonsu, dan basu san da sakkowar tasu ba. Sai dai kan wani yay magana Aunty Ummi ta ce, “Ba kai kaɗai drama ɗin nan ta isa ba Ammar harda mu ma. Shiyyasa ma su Yaya Ja'afar suka bar gidan, dama kuma jiran zuwan Uncle Nasiru kawai mukeyi muma. Idan Mammah nada zuciyar kawaici da haƙuri mu bamu san wannan ba, babu yanda za'ai maciji ya saremu a bakin rami mu sake maida ƙafarmu da tunanin bazai sake na biyu ba. Ai ko hausawa sunce sanin hali yafi sanin kama. Received atDan haka Uncle! Yaya kodai ku bashi shawarar ya koma inda ya fito, ko kuma ya nema masauki a wajen wannan gidan magana ta gaskiya”. Tana gama faɗar haka ta juya zata bar falon tana hawaye. Take mata baya su Ammar sukai suma. Mammah zata dakatar da su Uncle Nasiru ya girgiza mata kai alamar ta barsu.... Dole Mammah tai shiru, shi kuma ya miƙe yana sake faɗin, “Tasi'u tashi muje can gidana, mu basu lokaci nan da kwana biyu.” Daga shi har Mammah ɗin babu wanda yay jayayya, dan Uncle Nasiru yaya suke kallonsa uwa ɗaya uba ɗaya. Bayan wucewarsu shima Imran bai jima ba ya wuce gida abubuwa da yawa na masa kai-kawo a rai da zuciya...... (((★)))(((★)))(((★))) ★PRISON★ Yana komawa ɗakinsa ya zauna a gefen gadon sa yana kallon sojojin dake ƙoƙarin ɗaura tvn da suka kammala haɗawa a jikin bangon ɗakin. Baiyi musu magana ba, dan ko gaisuwar da sukai masa bai amsa ba a sanda ya shigo hannu kawai ya ɗaga musu. Suna kammalawa suka fice daga ɗakin tare da maida ƙofar suka rufe masa. Shima sai ya rufe idanu kamar yana barci amma ƙwaƙwalwarsa ce ta shiga aikin aunawa da lissafin abinda ya faru. “Facemask Analysis. Camara jikin agogo”. Ya furta a saman lips yana wani ɗan gajeren murmushi har lokacin idanunsa a rufe. A zuciya ya cigaba da ayyana suffar mutumin dalla-dalla da irin ƙwaƙwalwar ma'aikacin daya san aikinsa. (Fuskar bogi, agogo, tsayayyun idanu na masu busashiyyar zuciya da shekarun girma na tantance gwagwarmayar rayuwa na tsawon lokaci. Yanayin motsin ƙwayoyin cikinsu na ƙwararren operatives. Hakan na nufin wani daga cikin manyansu ne. Ba sabon shiga ba. Barazanar da ya faɗa. Sun ce suna sarrafa shugabanni… hakan na nufin akwai infiltration a cikin gwamnati. Wannan na iya zama sashin da ke kai rahoton Board of Inquiry. Ya ambaci makusanta. Hakan na nufin da damar su Imran ya zo wurina shekaru biyar da suka wuce. Yanzu kuma sune suka saka aka dakatar da shi. In dai haka ne to akwai idanu dake zagaye da Imran cikin rundunar soji ko wajenta, lallai Imran zai iya shiga haɗari akoda yaushe dan ko zai mutu bazai bisu fuska da fuska ba. Ya furzar da iska mai nauyi yana runtse idanu, dan Imran wani sashe ne na jikinsa da taɓashi tamkar ruguza jarumtarsa ne. Abu na uku tambayar su (Me yasa suka barni da rai har yanzu? Nima wannan tambayar ta jima a raina. Tabbas da nine a matsayinsu, zan kashe wanda nake tsoro musamman in haɗarinsa zai zama babbar barazana ga ƙasata bawai a karan kaina ba. Amma su suna bukata na a raye. Me yasa?) yay shiru na tsawon lokaci, sai kuma ya tashi zaune da ƙyau ya ɗauki pen da takarda ya rubuta wannan tambayar. _“They need me?. For what? To watch me? To use me? Or to fear me?”_ Pen ɗin ya kai saman lips ɗinsa da suka ɗan bushe dan yau yana azumi. Abu na huɗu (Wasan da suke cewa ya fara… hakan yana nufin wani babban shiri da suke da shi a wannan tsakanin kenan? Wani sabon hari ne?. Ko wata rawar juyin siyasa?. To amma ai basa buƙatar mutum kamar ni wajen gane kosu su waye?, ko ina matsalar?. Wannan kuskurensu ne ko ni ne ban fahimta dai-dai ba?) ya sake yin shiru alamar dogon nazari. Tsohon lokaci yana kai kawo da tunaninsa, sai kuma ya kai dubansa kan television ɗin da aka saka a ɗakin. Karo na farko ya miƙe yana ajiye littafin hannunsa da pen ɗin, gaban tvn ya isa, sai da ya gama duba ko ina na jikinta ya tabbatar babu camara sannan ya ɗauka remote ya fara searching channels, tashoshin dake cikin decoder ɗin da aka haɗata da ita duk zaɓaɓɓune. Domin guda uku ne kacal ba'a komai a cikinsu kuma sai abinda ya shafi labarai. Labaran ma ba kowane labari ba. Dan a yanzu dai kusan harkokin siyasa ne da campaign da aka fara kusan wata uku kenan. Idanun ya janye a hankali cikin salon yin luuu da su ya maida gefe da sakin murmurshin nan nasa na ƙeta. Sai kuma ya maida remote ɗin ya ajiye inda ya ɗauka ya koma bakin gadon ta sake zama.. Received Gaɓar da tafi tsaya masa ce ta sake maimaita kanta a brain ɗinsa. (Sun ce suna sarrafa zuciyar manyan. Idan haka ne, bayanan da Imran ya kawo min game da janar mai ritaya… dole sai na sake nazari. Domin kuwa wani daga ciki yana iya zama mai sarrafa Janar a gefe, da wannan damar kuma kaɗai za'a iya cimma Imran. Dan tabbas tunda har suka faɗa ya fahimci cewa ziyara ta farko da ta biyu na Imran sun haifar da damuwa a ɓangaren kungiyar shaiɗanun nan, shiyyasa ma suka hana shi cigaba da zuwa. Ya ɗan murmusa kaɗan, dan ya fahimci abu mafi mahimmanci har yanzu suna tsoronsa. Shiyyasa suka hana a ziyarcesa, suka hana yay communication da kowa, suka saka aka killaceshi inda baya ganin kowa sai masu tsaronsa dake kawo abinci dama duk abinda yake buƙata. Ya jima da gane a jikin masu tsaronsa akwai camara dake isar da saƙon shigarsu da fitarsu wajensa. Zuwan baƙon nan ma ba saƙon da yazo faɗa bane kawai maƙasudin zuwansa nan, suna son suga ko ya raunata a zuciya zuwa yanzu. Suna son su gane ko ya ragargaje da raunin kaɗaici. Suna son su tabbatar ko har yanzu yana da ƙarfi daga irin ƙarfin da suke tsoro. Gaba ɗaya ma sai yaji ya sake raina wayonsu. Dan da da gaske, suna da ƙarfin ikon da suke faɗa, ba zasu zo su gaya min ba. Babu mai saƙon barazana da ikon cikakke sai wanda yake jin tsoron wanda aka aika wa saƙo. Yay ƙwafa, saboda wannan tunanin ya ƙara masa ƙarfin gwiwa, da fushi, da nunin ya sake tashi tsaye da shirye-shiryesa. Dole kuma ya aikama Imran saƙo batare da jinkiri ba...........✍️ [01-16, 11:37] +234 703 449 6321: KIƊA A RUWA 2 26 ..........KWANA UKU da dawowar Mammah suka karɓi baƙuncin ƴan Bauchi da sukazo sunan Aunty Mommy. Gwaggo Khadijah, Gwaggo Alawiyya, da Gwaggo Nanah. Sai matar Uncle Jamilu da wannan ne karonta na farko da tazo. Dan tun abinda taima su Mammah ɗin a wancan shekarun take jin matsanancin kunyar zuwa inda suke. Sai dai har cikin ranta taji nadama. Musamman da ayanzu su Mammah ɗin ne riƙe da rayuwarsu tunda su Ja'afar ne suka buɗema Uncle Jamilu babban shago kayan sakawa a can Bauchin ƙyauta, da shi suke ci suke sha. Sannan kuma suka ɗauki nauyin karatun yaransu a makaranta mai ƙyau. Gwaggo Nanah kam ta fita zakka a cikin ƴaƴan Inna, tana iya ƙoƙarinta dama tun ma suna cikin wahalar rayuwa kamar yanda Gwaggo Khadijah da Gwaggo Alawiyya keyi. Sai dai tsoron ƴan uwanta su Yaya Babba ke hanata zuwa inda su Mammah suke. Wannan karon kuwa itama sun mata halin nasu, dan mijinta ya gudu ba'a san inda yake ba shekara biyu kenan duk sun ƙi taimaka mata, ga wahala tana ciki ita da yara. Babu mai taimaka mata sai Uncle Jamilu da su Gwaggo Khadijah ɗin. Shiyyasa ta yanke shawarar zuwa sunan nan danta sanar ma Mammah halin da take ciki ko zata samu wani taimako. Kuɗin mota ma Uncle Jamilu ne ya biya mata. Ba ƙaramin daɗi Mammah taji da ganinsu ba. Musamman Gwaggo Nanah da matar Uncle Jamilu Badiyya da suketa ɗari-ɗari suna jinjina hukuncin UBANGIJI da ganin gidan da Mammah ke ciki a yau da zuri'arta. Lallai duniya budurwar wawa, wanda yace shine kuwa ba shi ɗin bane ba. Tuni Mammah ta saka su Kulu masu aiki suka gyaro musu ɗakunan baƙi, dan sunyi isowar wuri lokacin sha ɗaya na safe, sunce tafiyar asuba sukayi dan mota suka ɗakko kai tsaye. Mammah dake ta farin ciki ta ce, “Ku fara yin wanka da ruwa mai zafi sai kuzo ku karya. Bara kiga nasa a kakkaɓo min yaran nan duk suna gado jiya sun raba dare ne suna shargallen su”. Gwaggo Khadijah tai ƴar dariya da faɗin, “Aike da gayyar nan taki Maman Ma'aruff sai ALLAH. Kinga barsu suyi barcinsu, muda ba yau zamu koma ba. Anjima ma wata hidimar ce ta bikin suna a kansu”. “Kamar ko kin san harda fati suka shirya wai. Biebah ce kawai ta iya bin su Lailah gidan maijegon, yanzu babu jimawa suka fice suma dan jiya sai goma suka dawo”. Yanzu kam Gwaggo Alawiyya ce ta ce, “Kai waɗan nan yara ALLAH dai ya saka musu da alkairi. Wlhy samun surukai irinsu sai an tona Addah.” “Ai su Shariffa sun wuce surukai ƴaƴane Alawiyya. Babu abinda zan cigaba da musu sai addu'a da fatan suma ALLAH ya basu masu yi musu”. Gwaggo Nanah dake jinjina kai ta ce, “Wlhy ki musu ki ƙara muma muyi musu, ga gidan Yaya Babba can su Haire su da surukai ba arziƙi. Jiya matar Haƙilu kamar zatai dambe da Haire akan ɗanta, ke bakiji wannan tujara ba abin kaico”. Murmurshi Mammah tayi, saboda a saki zancen ta ce, “ALLAH ya ƙyauta to, ai zamanin ne ya zama abin tsoro sai addu'a kawai. Kunga kuyi wankan kuzo ku karya hirar tafi armashi”. Godiya suka yi ta juya ta fita. Dukan su suna jin ƙaunarta a ransu, Badiyya kam kunyarta take ji sosai shiyyasa tunda suka gaisa tai shiru kanta a ƙasa. Sarai Mammah ta fahimceta, dan haka ta ƙuduri aniyar cire mata abinda ke ranta gaba ɗaya, dan ita babban fatanta ta haɗe kan zuri'ar Abdul-rasheed ba rabuwar kansu ba.... ★ Sai sha biyu su Nimrah suka tashi da ƙyar, shima sai da Mammah tazo da kanta ta tashesu. Dan suna yin sallar asuba suka koma gado. Aiko sai shagwaɓa suke mata wai ta barsu sai ƙarfe ɗaya sannan. “Shike nan kun fasa zuwa gidan sunan kenan? Ai da nasan haka ne sai na tadaku kun wuce Tahafiz. Ga ƴan Bauchi can tun sha ɗaya suka iso ku kuna nan kuna barci”. Tuni duk suka watsakke, cike da farin cikin jin zuwan ƴan Bauchi. Zasu nufi ƙofa a guje Mammah ta dakatar da su. “Kai kuji min ƙazaman banza. Haka zakuje musu da kayan barci? Ba brush kamar wasu ƙazamai. Maza ku koma ku gyara jikinku, wata taje ɗakin Biebah yanda zakuyi sauri”. Received Cike da farin ciki sukace to. Mammah ta fito tana murmurshi. Koda ta dawo falon wajen su Gwaggo Alawiyya ta samu su Ma'aruff sun iso gidan. Dan tun ɗazun ta sanar musu sukace zasu zo yanzu. Sai ko gasu da ledoji niƙi-niƙi na kayan ciye-ciye. Fuskokinsu washe da murmushin ganin gwagwgwannin nasu. Badiyya na sinƙe-sinƙen kai ganin yanda suma basu nuna mata komai ba kamar Mammah sai ta ware aka fara gaisuwa da tambayar yara. Yaya Ja'afar ya ce, “Haba Gwaggo, kwa taho ku kaɗai duk babu yara? Bayan kun san ba ganin juna ake ba tsahon lokaci sai irin haka ta faru”. “Makaranta tasa haka Ja'afar, amma in sha ALLAHU idan anyi hutu sai su zo. Tunda kudai kun tattaramu kun watsar, yaushe rabonku da Bauchi balle Maiduguri?”. “Dama idan sunje Bauchin ba ganinsu muke ba Adda Khadijah, iyakarsu gidan Yaya Jamilu da Adda Alawiyya. Dan nidai sau biyu suka taɓa zuwa min lokacin rasuwar Inno surukata, da ciwon Ahmadi”. “Munyi laifi Gwaggo Nanah, amma kiyi haƙuri zamu gyara in sha ALLAHU. Wani lokacin abubuwan ne ke yawa. Mafi yawan lokuta kuma zuwa Bauchin kasuwa ke kaimu. Ki tambayi Aunty Badiyya sau da yawa shima Uncle Jamilu a kasuwa muke samunsa ba gida muke zuwa ba. Itama Gwaggo Alawiyya takan jima bata gammu ba. Maiduguri ne dai kam ma zamuce muna shiga dan ziyara kai tsaye”. “To na gamsu, amma dan ALLAH a gyara, mun san mu masu kuskurene a gareku, amma kuyi mana afuwa kunji, Yaya Abdul-rasheed mutum ne mai son zumunci da Adda A'isha da Adda Yakura, na tabbatar kuma akwai wanan jinin alkairin nasu a tare daku, kar ku biyema aikin son zuciyar wasunmu ku watsar damu gaba ɗaya. Suma lokaci zai yi da zasu yi nadamar abinda suka shuka. Dan har ma wasu sun fara, Yaya Babba a tsakanin nan babu abinda yake sai tafka asarori kala-kala, ga yara cike da gida, mata har huɗu. Yaya Haruna ne ma za'ace da ɗan sauran damshi-damshi. Shi ko Yaya Garzali ma yaje ya tare saudia aikatau ƙiri-ƙiri ko takan matan baya bi sai ya gadama.” Sosai zancen ya girgiza su. Sai dai basu ce komai ba face ALLAH ya ƙyauta. A haka Ammar ya shigo shima da Mu'azz. Nan fa falon ya sake lacamewa da farin ciki. Sai kuma gasu Nimrah na fitowa cikin kwalliya tsaff suna baza ƙamshin turaren da suka satarma Aunty Biebah na SHUWA INCENSE AND MORE +234 704 229 3387. Cike da farin ciki suka rungume Gwaggo Alawiyya da Gwaggo Khadijah dan su suka sani sukam. Abin birgewa bazaka taɓa cewa ba jininsu bane su. Sun gaida su Gwaggo Nanah suma. Suka amsa musu da kulawa duk da basu san alaƙarsu da gidan ba. Garama Fiddo ƴar Aunty Mommy data kwana a gidan itama, tunda sun jajje Bauchin ita. Gwaggo Khadijah ta ce, “Oh ni Dije Maman Ma'aruff ƴan matan nawa duk sun miƙe. Kaga yara kamar wasa sun ƙosa. A wannan sai aure”. Caraf Mu'azz ya ce, “Tab ɗin wazai kwasa Granny? Wannan gayyar ciwon kan da basu iya komai ba sai dambe da neman masifa da ƴaƴan mutane”. Baki duk suka tura gaba. Gwaggo Khadijah ta ce, “Kunga ƙyaleshi ƴan uku Ko nace ƴan huɗu dan banbu Bintu ne. Ai ana yin auren duk zaku daina ko. Kuma dai ai kowa da ƙuruciyarsa, shima idan za'a faɗi abinda yayi ai sai kowa ya gudu”. Dariya suka shiga yima Mu'azz suna masa gwalo, shiko yana hararsu da musu alamar zai kama su. Su Yaya Ma'aruff dai na murmurshi ne, Yaya Ammar kam dining ya nufa yana faɗin shifa yunwa yake ji, mi aka dafa ne?. Miƙewa su Nimrah sukai suma suna faɗin yunwar suke ji. Daga haka suka koma kan dinning ɗin harda su Mu'azz aka bar su Yaya Ja'afar suna hira da su Gwaggo Khadijah..... <<%>><<%>><<%>> Da yamma shagalin suna aka sha sosai a gidan Aunty Mimi, duk da kuwa haihuwa ce ta huɗu tayi. Babu ƙarya su Nimrah sun cashe da rawa iya iyawarsu. Kasancewar hall aka kama iyakar kuma mata ne kawai a wajen dan ko su Mu'azz basu shiga ba sai abin ya ƙayatar. Ƙarfe shida aka tashi saboda sallar magriba. Nan fa motoci suka fara ɗibar mutane zuwa gidajensu. Su Nimrah dai yau a gidan Aunty Mimi zasu kwana. Dan haka sukabi ƙanin mijinta da yazo kwasar yaranta dana family ɗin mijinta. ReceivedDuk da dai da farko ca sukai su bazasu shiga cikin yaran ba, sai da Aunty Shariffa ta fara musu faɗa da tabbatar musu zako ta kaɗa kansu zuwa gida sannan suka nutsu saboda suna son zuwa can ɗin su ƙarasa weekend ɗin su. Ga Bintu kuma ta ƙaru sun zama su huɗu yanzu. Haneef dake matuƙar son Ruƙayya na sharewa yana faman murmushi yace su jira shi ya kai yaran ya dawo to. Feedo ce ta amsa masa da “To Uncle”. Su Ruky kam aka wani ɗauke kai gefe. Murmurshin shaƙiyanci Nimrah tayi, tare da ɗagama Bintu gira ɗaya cike da gulma. Aiko suka kwashe da dariya. Ruky da tasan da ita suke ta balla musu harara da jan tsaki zata bar wajen Nimrah ta riƙota........✍️ Received at 6:38 PM[01-16, 11:37] +234 703 449 6321: KIƊA A RUWA 2 27 .........“Sorry Trouble Buddy na. ALLAH ke ɗin ce kin cika wulaƙanci, Uncle Haneef fa ya haɗu ALLAH. Amma kiyita wani shan ƙamshi. Dan ALLAH ko kaɗan ki dinga kulashi mana, ALLAH idan ya ganki zakiga duk bakinsa yaƙi rufuwa”. “Ai shiyyasa bazan kulashin ba. Ni fa bana son susun namiji haba. Mutum babu wani jan aji. Kuma ni an faɗa masa za'a min aure ne yanzu mtsoww!!”. Bintu dake dariya ta ce, “Baby ai kece zaki saita shi yanda kike so. Amma kina wani yayyarfashi, jifa da salla yanda ya mana siyayya”. “Mayya dama ke ai kwaɗayi ne zai kashe ki ke da Ninah”. “Ya kashe mu dai, tunda tare muke”. Cewar Nimrah tana hararta. Ramawa tai itama, sai dai dai-dai nan Haneef ke dawowa dan haka hirar tasu ta tsaya. Fitowa yay da kansa ya buɗema Ruky gaba, zata zille ta shiga baya inda su Nimrah ke shirin shiga suka turata suna ƙumshe dariya. Juyawa Haneef yay ya kallesu da musu jinjina yana murmurshi. Daga haka ya rufe mata ƙofar ya zagaya dan suma har sun rufe. Yana fara tafiya a titi ya ɗan kalla Ruky, cike da son birgeta ya ce, “Muje shan Ice-cream ne Baby?”. Kai ta girgiza masa alamar a'a. Sai ya ɗan marairaice fuska, tare da maida lallonsa kan su Nimrah dake baya ta mirror. “Yaran Uncle muje mu sha ice-cream ne?”. Cike da iyayi Feedo ta ce, “Yes Uncle”. Nimrah zatai magana Bintu ta rufe mata baki, dan sun san bakinta ɗaya da Ruky. Ganin zata fisge itama Feedo ta ɗaura nata hannun akan na Bintu suka haɗu suka danne Nimrah. Sai da ta sakar musu wasu shegun mintsini masu zafi suka saketa kowanne na sosa wajen. Badan Nimrah da Ruky sun so ba akaje wajen shan wannan ice-cream dai. Haka ya jasu har ciki kowacce ta zaɓi flavor ɗin da take so. Ya ƙara musu da snaks. Duk yanda suka so ya maida su gida ƙi yay, haka ya janye ra'ayinsu suka zauna a wajen. Sai dai rashin sabo ya sasu kasa sakin jiki su dukansu. Dan abu ne da su dukansu ba tarbiyyarsu bace. Shi ko yanata tsiyaya musu zance da ɗaukarsu hoto da wayarsa iPhone. Ganin fa an fara sallar isha'i hankalin Nimrah ya tashi. Dan in har ka gansu a waje irin wannan lokacin tabbas da wani a cikin Uncles nasu ne ko Ya Mu'azz ko Aunty Biebah ko kuma sun raka su Aunty Lailah anguwa ko Ammie. Amma basu kaɗai ba balle wannan da saurayi ma wai. “Nimrah ya naga kin miƙe?”. Haneef ya faɗa yana kallonta. “Uncle Haneef kayi haƙuri ka maidamu gida. Wlhy idan Mammah taji zatai mana faɗa, balle Daddy ko su Uncle's”. “Haba-haba ai in sun san nine babu wani faɗa da zasuyi”. Miƙewa itama Ruky tayi, hakan yasa suma su Feedo duk suka miƙe. Kafin ma Nimrah ta bashi amsa Feedo ta ce, “Wlhy Uncle koni Abbana ya sani ubana zai ci. Muje ɗin kawai ma ƙarasa a gida”. Babu yanda ya iya dole ya miƙe, ya tayasu tattare kayan suka fito. Kamar ɗazu yanzu ma dole Ruky gaba ta shiga. Cikin ƙankanin lokaci ya iso gidan Aunty Mimi da su. Yay horn maigadi ya buɗe masa gate ya shige. Suna fitowa a motar maigadi ya iso inda suke. Kai tsaye gaban Nimrah ya isa yana miƙa mata ledar hannunsa da faɗin, “Hajiya gashi wani yace a baki. Yata jiran dawowar ku amma yaji shiru yanzu babu jimawa yabar wajen nan.” Ba ita ba hatta su Ruƙayya da mamaki suke kallonsa. Cikin kasa daurewa Nimrah tace, “Kuma ni Nimrah yace a bamawa?”. “Tabbas ke yace, yace sunansa Kamal malaminku na islamiyya”. Ruky ce ta amshi ledar tana faɗin, “Wato shima Sayyadi Kamal ɗin nan ɗan naci ne fa na lura”. Daga haka tabar wajen fuuu. Tsaff su Nimrah sun fahimci fushin Haneef tai amfani da shi akan Kamal. Dan haka suka wayance da masa godiya suka shige cikin gida. Sun sami sauran dangin mijin Aunty Mimi da basu kai ga wucewa ba. Suka gaishe su suka wuce ɗakin da suke sauka in har sunzo gidan. Dama can suka kai kayansu da daddare. Ƙaton gado ne da zai iya isarsu koda su shida ne a ɗakin, sai wadrobe da mirror, sai ƙofar bayi. Kayan hannunsu duk suka ajiye suna zubewa a gadon kowa na faɗin wash, dai-dai nan Ruky data rigasu shigowa ta fito daga bayin alamar har tayi alwysSuma duk miƙewa sukai, dan rashin yin sallar akan lokaci na tsaye a ran kowannensu. Bintu ce kawai ke period dan haka taja ledar snaks ɗinsu ta fara ci tana faɗin, “Bari muga mi Sayyadin ya aiko mana da shi shi kuma”. Tsaki Nimrah tayi a karo na farko tana shigewa bayi abinta. Fiddo ta sanya dariya dan Ruky ma harta kabbara salla. Dariyar su Bintu data cika ɗakin ya saka Nimrah fitowa da sauri, itama Ruky dai-dai tana idar da sallar ta juyo tana kallonsu. Litattafai ne a ledar saƙon Sayyidi Kamal suka nuna musu. Feedo ta ce, “Wannan fa shine auren ustaz ɗin, kaga wata lukutar jaraba wai saƙon littafai. Ninah kina cikin yanayi gaskiya”. Nan ma dariya suka sanya harda Ruky yanzu kam. Dan haka Nimrah ta watsa musu harara ta kabbar sallarta itama. Koda ta idar sun gama mata shaƙiyancin nasu, dan haka bata sake tada zancen ba ta haye gadon ta kwanta wai kanta ke ciwo. Da ƙyar suka lallaɓata ta zauna suka ƙarasa shan Ice-cream ɗinsu da snaks ɗin bayan Feedo ta idar da salla itama. Dan haka koda Aunty Mimi tai kiransu suzo su ɗeba abinci sukace mata sun ƙoshi. Bata takurasu ba dan taga abinda suka shigo da shi, ta kuma san aikin Haneef ne...... <<<<<<(⁠✷⁠‿⁠✷⁠)>>>>> ★CAMPAIGN★ Kwanaki 100 na campaign suna gab da cika, dan kuwa ana satin ƙarshe na kammala taron kowane kamfen. Dan haka amsa kuwwar cikar kwanakin tamburan siyasa na gab da cika, tako ina ƙasa ta kara hargitsewa dan kowa burinsa satin ƙarshen nan ya tumfayesa da zuciyar yan kasar. Baka iya jin komai sai sautinkan waƙoƙin da aka rairana ƴan siyasa. Yayinda hankalin matasa kacokan ya koma can. Wasu ma sun ajiye harkokinsu da sana'o'in su ne kacokam. Kamar dai yanda aka saba alƙawuran nasu guda huɗu ne ga al'ummar ƙasa a lokacin da suke kan munbarin campaign. Zamu gyara muku harkar karatun, zamu inganta wutar lantarki, zamu wadata ku da ruwa, zamu gyara asibitoci. Cikin rashin lissafi da auna abubuwa a yanda ya dace, da taro da kwabon da ake raba mana mu talakawan ƙasa da ɗan sabulai da zannuwan ɗaurawa mai hoton ƴan siyasar a jiki sai kaji mun sallama muna bada kai bori ya hau. Babu ruwanmu da tantance wane shugaban ya dace damu? Mi muke so a ƙasar da kawunanmu bayan waɗan can lissafin huɗu da ko a karatu sukazo ya kamata ace mun haddace su tsaff zuwa yanzu daga daɗin bakinsu mu nemo cigabansu. Amma ina babu batun tantancewa, a wasu wajajan ma siyasar ta haɗa rigima ne tsakanin ƴan uwan juna saboda ni ina son wannan wane ɗan uwana yana son wancan ba jam'iyyar mu ɗaya ba. Wasu har gaba zakaga ta ƙullu mai girma a tsakaninsu. Yayinda su ƴan siyasar da sukeyi domin su suna can tare suke shan shayi, tare suke ƙulla mai fishshesu musamman akan abinda zasu ribantu da shi game da kuɗaɗen da suka kashe wajen jawo ra'ayinku idan sun haye. Wanda ma bai haye ba akwai hanyoyin da za'a bi dan maida masa wahalarsa ta bayan fage kune a ruwa... Alhamdullahi duk da irin tasu tafiyar bata banbanta data Janar Yusuf ba a yau kasancewar a ƙarƙashin damarsu ya ke shima a siyasar kamar saura abinda shekarun baya suka zo da shi wajen campaign shima dai shine a yau yake zuwa da shi. Kuma Alhamdullah zamu ce akwai nasara a al'amarin dan yana da magoya baya sosai a cikin jam'iyya da al'ummar gari. Abinka da soja, a kwanakin kai-kawon duk da wahala da jigatar rashin barci dana hutu zuciyar maza a tsaye take da ƙyaƙyƙyawan fata. Tun ana farkon satin nan da sukai zama da Imran ya kuma gana da Uncle Nasiru basu sake haɗuwa ba. Dan a zahiri Imran baida alaƙa da siyasar Janar. Gara-gara ma Uncle Nasiru har campaign ya rakashi sau biyu. Duk wani abinda ya dace su tattauna sun kammala sun ajiye kundin shirinsu gefe har sai ta ALLAH ta kasance. Wato aci zaɓe ko a faɗi... Tsahon kwanaki sun cika cir, awanni 48 ya rage a fara jefa kuri'a, dan haka batun campaign komai ya lafa a koma jiran ranar jefa kuri'a da gwamnati ta riga ta fitar kuma kwanaki 2 ne kacal, dan yau alhamis.... ★_______★ ★RANA BATA ƘARYA Received at 7:39 P Yau safiyar asabar. Safiyar zaɓen shugaban ƙasa. Duk wani masoyi na yan takara a kowane ɓangare jikinsa na'a farce ne. Ba yan takara kaɗai ba da zuri'ar su yan kasa kansu kowa hankalinsa nakan fata ga wanda yake so. Dan haka kasar ta wayi gari a yanayin sai addu'a kawai. Wasu cike da fata, wasu cike da tsoro duk da tako ina jami'an tsaro na aikinsu ne. A ka'ida daga shekara sha takwas ne za'a iya saɓe zuwa sama. Dan haka su Nimrah basa cikin masu jefa ƙuri'a. Amma ganin su Mu'azz zasu suka maƙale zasu je. Mammah kam Daddy Imran da kansa yazo ya ɗauketa ita da Hajjo ya kaisu suka jefa kuri'arsu da wuri sosai tare da Janar Yusuf Shu'aibu Tafida da iyalansa. Duk da dai ba kai tsaye Daddy Imran ya fito a tawagar janar din ba saboda bada ƙafa. Amma janar na jefawa da iyalansa suna a rukuni na biyu da suka jefa suma. Daga can Mammah tabi Hajjo suka wuce can gidan dan suma su Gwaggo Khadijah zasuje gaida Abba, amma su basuje jefa kuri'a ba daga gida za'a kaisu can tunda Mammah ce ta riƙesu tace sai an gama zaɓe zasu koma gida, kuma acan suke da mazaɓa.........✍️ [01-16, 11:37] +234 703 449 6321: KIƊA A RUWA 2 28 ..........A ƙafa zuri'ar Mammah suka fita domin zuwa jefa kuri'a dan anan cikin street ɗinsu ne mazaɓar tasu take, dan babu wanda aka bari a gidan har su Afrah. Kasancewar anguwa ce ta ƴan gayu babu hayaniyar mutane, wasu ma duk sun koma state ɗinsu jefa kuri'a a can yasa anan ɗin babu yawan jama'a babu hayaniya balle damuwa. A nutse su Uncle Ma'aruff da su Aunty Shariffa suka jefa har zuwa kan Mu'azz karamin gidan. Kuma alhamdullahi dukansu Janar Yusuf suka dangwalawa. Suna kammalawa suka juya zuwa gida abinsu. Nimrah da Ruky ne a gaba, suna tafiya da baya-baya Mu'azz na musu video dan Nimrah harda Teddy ɗinta ta fito. Dan haka su Abees keta binta dan suna son taɓa teddyn magen. Daga ita har Ruky abaya ce a jikinsu, su duka sun musu ƙyau, tare da fidda tsayinsu masha ALLAH... ★WASHE GARI aka tashi da batun sakamakon zaɓe. Hankalin su Nimrah ba'anan yake ba. Bama kuma su fahimci miye damuwar ƴan gidan da batun sakamakon zaɓen ba da suketa bibiya tun jiya. Dan kamar wasa ranar ma a gaban television suka yini. Har kuma akai sallar magriba babu wani bayani, sai da aka dawo sallar isha'i suna cikin cin abinci aka sanar..... A wannan daren ba gidan Mammah kawai ba ake jiran jin sakamakon zaɓen shugaban ƙasa ba, kusan ƙasar gaba ɗaya a kowanne gida hakan take, dan yau Daddy Imran salla kawai ke sakashi matsawa a gaban television amma ko abinci sai Anmie ta matsa masa ma yake cinsa, shima laumomi ne kawai. Ga Asma'u da Khalifa nane da shi suma. Zuciyarsa kam cike take da tsoro da fargaba. A wasu gidajen kuwa irin namu na talakawa an kunna fitilu ƴan uwa da abokai sun taru a gaban rediyoyi suna jiran murya ɗaya tak ta shugaban zaɓe, murya ce da zata faɗa musu ko tarihin ƙasar za’a sake rubutawa ko zai sake maimaita kansa ne da wanda ba zaɓinsu ba. ★★★ Ko'a gidan tsohon Janar Yusuf Tafida ya ɗauki wani irin shiru mai nauyi. Yana zaune a kan kujerarsa mai laushi, hannunsa riƙe da remote, television ɗin a kunne amma zuciyarsa na bugawa da ƙarfi. Matarshi, Hajiya Zainab, tana zaune a gefensa, hakama kaf yaransa har mazan dake da mata na a falon zaune zagaye dasu kowa zuciya na rawa da addu’a, dan sun san yanda mahaifinsu ya ƙwallafa rai akan shugabancin nan yana buƙatar sanda za'a sanar da wa ya samu ace suna kusa da shi. Hakan zai bashi ƙarfin gwiwar amsa daga abinda ƙaddara zatazo da shi. Tunda shugaban zaɓe ya fara magana kusan a lokaci guda numfashin biliyoyin al'ammar ƙasar ya tsaya cak. _“A bisa sakamakon da aka tattara, ɗan takarar AGS Party, Honourable Yusuf Shu’aibu Tafida… ya lashe zaɓen shugaban ƙasa.”_ “Ya arrahim!”. Hajiya Zainab ta faɗa tana mai fashewa da kukan farin ciki tare da miƙewa ta rungume Janar da ke kusa da ita kamar yayi sumar zaune. Sai da ta sake furta, “Alhamdulillah Daddyn Deen! Alhamdullahi!. ALLAH ya baka, ALLAH ya cika maka burinka, ALLAH ya baka wannan ne don ka gyara gaskiya!”. A hankali Janar ɗin ya lumshe ido, zuciyarsa cike da wani nauyi mai girman gaske, nauyin da yake jin tamkar ya ɗauka daga yanzu nan har zuwa shekaru da yawa. Lokacin da ya buɗe ido sai kawai ya zame yay sujida, ganin haka itama ta bishi, hakama yaran da gaba ɗaya suka kacame da ambaton Alhmdllh duk sai suka bisu.... ★★★ A gidan Mammah ma lokaci guda falon yay wani irin shiru na sakan, kafin su Yaya Ma'aruff su kacame da ambaton kalmar Alhamdullah. Sai da suka ga Mammah ta tafi sujida sannan suma duk suka bita har su Ruky. Mammah ta jima bata ɗago ba saboda hawayen da suke zubar mata. Koba komai tana ji a ranta nesa tazo kusa in sha ALLAHU. Sai da ta goge hawayen tas sannan ta ɗago tana murmurshi. Su dai su Yaya Ja'afar na mamakin yanda Mammah ke son janar ya samu kujerar nan, amma basu taɓa tambaya ba, yanzu ma kuma basu tambayar ba. Kawai suna ganin da Yaya Imran na son shi ne dai. Kuma Dada ma sanda yana nan yana girmama al'amarinsa matsayin ogansa...... <<%>><★><<%>> Received at 4:21 PM Shima dai a ɓangaren Daddy Imran tamkar Janar ana sanarwa yi yay tamkar ha suma a zaune. Duk ihun da Khalifa da Asma'u keyi baima jisu ba sai da Ammie data zuba masa ido tana murmushi ta kama hannunsa ta matsa a cikin nata. Wani nannauyan numfashi ya kawo hawaye na cika masa ido. Ya kalli Ammie dake lallonsa cikin ido tana murmushi, dan duk da bai taɓa fitowa ya sanar mata shirinsa tsakaninsa da Janar ba tana tsintar wasu abubuwan nasu ta waya idan suna yi. Yau kam ko kunyar yara baiji ba ya jawota jikinsa ya rungumeta, a haka cikin dabara ya share hawayen da suka cika masa ido. Kafin ya saketa ya tafi sujida shima. Sai suma duk suka bishi, yana ɗagowa yayma su Asma'u alamar suzo gareshi, suma su biyun ya haɗasu ya rungume dan auta barci yake. Sai da ya sake su suna masa congratulations yana gyaɗa musu kai da ɗaukar waya dan bakinsa ma ji yay ya masa nauyi. Kai tsaye layin janar ya kira duk da baida tabbacin samu, dan yasan a yanzu duk wani masoyinsa abinda yake ƙoƙarin yi kenan... Tabbas hasashen Daddy Imran akan Janar haka ne, dan wayoyine keta rige-rigen shigowa wayar sa a dai-dai wannan lokacin, sai dai ta yayansa kawai ya ɗaga sai ga ta Imran ma. Sunan da ya gani yasa zuciyarsa ta tsaya na ɗan daƙiƙai. (Imran....) Sai yaga sunan na koma masa bibbiyu tamkar haɗe da sunan Haysam. Sai da ya lumshe idanu ya sake buɗewa sannan ya ɗaga yana kaiwa kunnensa. Daga sallama abu na biyu da Daddy Imran ya furta shine, “Sir… mun yi nasara Alhamdullah. Subahanal-lah. Allahu-akbar. ALLAH ya tabbatar da alkairi, mulki jarabawa ce mai girma, ina roƙon UBANGIJI ya dubi tsarkin zuciyarka, da ƙyaƙyƙyawan fatanmu da ƙyaƙyƙyawan zaton da muke maka yay riƙo da hannayenka wajen baka damar sauke nauyin al'ummar wannan ƙasa gwargwadon iko. Duk wanda zai kasance da kai a cikin wannan sha'anin mulkin in har bazarana ne shi ga sauke hakkokin mutane koda wanene ALLAH ya tauyeshi ta inda zai rasa ƙarfin iya yin komai. UBANGIJI ya zama gatanka, bangon jinginarka, mafakarka, damu baki ɗaya. Once again, Congratulations, Sir.” “Thanks you Imran. Amin ya rabbi Jazakallahu khairan. Imran ka san wannan nasara ba tawa ba ce. Tawa da taka ce. Ta Haysam ce. Ta gaskiya ce.” Hawaye ne suka cika idanun Daddy Imran daga can, muryarsa na rawa ya ce, “Na gode, Sir… na gode da bama wannan YAƘIN daraja da kake yi.” “Yaƙin Haysam yaƙinmu ne ƙasa gaba ɗaya, wanda bai sani bane ko bai fahimta bane kawai keja da baya. Ka shirya, dan tun gobe idan ALLAH ya kaimu nake so ka fara haɗa min duk bayanan shari’ar Haysam tun daga farkon ranar da aka fara har ƙarshe. Ba zan shiga gidan gwamnati ba tare da na duba gaskiya ba. Lokaci ya yi da za mu dawo masa da mutuncinsa tare da namu muma Imran. Dan haka kwana ɗaya kawai zanyi da shiga gidan gwamnati Haysam ya fito in sha ALLAHU”. Daddy Imran ya gyaɗa kai, hawayen da yake ta riƙewa tun ɗazun na sauka masa. Muryarsa ta shaƙe a cikin maƙoshinsa dake kai-kawo da nauyin shekaru takwas na zafi ya furta, “Sir! Sai nake jin kamar ina mafarki ne irin wanda na sabayi. Dan ALLAH idan barci nake kada ku tada ni”. “Ba barci kake ba Imrana. Gaskiya bata da lokacin jira. Dole tun a yau mu tunawa kammu akwai wani mutum da ba zamu bari ya cigaba da kwana cikin duhu ba bayan ALLAH ya bamu wannan AMANAR, maza kaje, jeka ka fara shirin fitowar gwarzon haziƙin jarumin soja mai gaskiya da kwatanta gaskiya akan kowace gaskiya duk ƙarfinta.” “Thanks you Sir! Thanks yo...” Daddy Imran ya kasa ƙarasawa saboda yanayin da yake ciki misaltashi sai UBANGIJI. Ji yake tamkar zai faɗi sai da ma Ammie ta riƙeshi suka zauna ta miƙa mashi ruwa. Dama ta kora su Asma'u suje suci abincin dan kaf ɗinsu yau babu wani abincin kirki a cikinsu saboda uban gayya bai ci ba hankalinsa nakan television yini guda. Tambayar da Ammie ta jefa masa a karo na farko game da al'amarin yasa Daddy Imran kallonta cikin ido. Wani sassanyan murmushi ya sakar mata, batare da ya buɗe mata ba a dunƙule ya furta, “Akwai wani mutum guda dake bina bashi Hafsat, bashin adalci, bashin ƙauna, bashin zuminci. Received at 4:21 PMReactions:Kuma lokaci ya yi da zan biyashi koda da kwatantawa ne.” “ALLAH ya cika maka wannan buri Daddyn Khalifa”. “UBANGIJINA ya cika min sai dai tabbatarwa”. Ya faɗa cikin salon raɗa da rungumeta a jikinsa..... ============= ★PRISON★ A kwanakin farko na kawo television ɗin ɗakinsa bai maida hankali akan zaman kallonta ba, dan lissafinsa nakan haɗa kalaman vistor ɗinsa da musu fashin baƙi a farashin mutane masu hangen nesa da basu raina bincike irinsa. Abu uku kawai da aka turke tvn da ita ne ya fara tasirin jan hankalinsa gareta dole. Sun saka mata security ta yanda bata kasuwa, bai iya rage volum, bai canja tasha daga ukun nan kacal duk da kuwa akwai remote. Duk da basu sakata da ƙara mai takura ba kasancewar sa mutum mara san damuwa da hayaniya sai da ta fakurashi a kwanakin farkon. Sai daga baya daya fahimci an kawota ne garesa dan tai masa irin wannan takurar ai sai ya dake ya ajiye komai gefe har a kwana na huɗu ya maida hankali a kallon fashin baƙin masana akan taron campaign ɗin da aka rufe, a bazata yaci karo da na Janar Yusuf Shu'aibu Tafida ne a gaba. Duk da bawai akan Janar ɗin masu fashin baƙin ke tattaunawar ba, suna tattaunawa ne akan mabiyan ɗan takara, inda daga ƙarshe suke faɗin alƙaluma na sake nuna tsohon Janar dake gaba wajen tara masoya a duk jahar da yaje. Wannan shine karo na farko daya fara bama tvn hankalinsa, daga ranar kuma ya cigaba da bibiyar komai daki-daki, har hakan ya bashi damar fara tantance kowace fuska dake tare da Janar Yusuf dama sauran ƴan takara tun daga na shugaban ƙasa har zuwa shugabannin jihohi. A haka aka gangaro har ranar zaɓe, duk yanda abubuwan ke gudana nan ma yana biye, sai ta kai har ƙirga ƙuri'u ya bibiya. Sai dai a yau da aka tashi da jiran faɗar sakamako ya yini da ciwon kai saboda matsawa kansa da ayyukan ƙwaƙwalwa da yay a cikin satin nan gaba ɗaya. Dan haka bai wani maida hankali ba sosai ga television ɗin, bayan ma ya idar da sallar isha'i yay zaman fara karatun Alkur'ani ne, kasancewar tvn ba kasuwa take ba, ba rage ƙara take ba a bazata bayanin shigaban hukumar zaɓe ya shiga cikin kunnensa. Cak harshensa ya tsaya dai-dai da bugun zuciya na sakanni, kafin ya iya ɗago manyan idanunsa zuwa kan tvn ya saukesu akan fuskar ɗan jaridar dake maimaita kalmar.........✍️ Received at 4:21 PM reacted[01-16, 11:37] +234 703 449 6321: KIƊA A RUWA 2 29 ..........“Wow! Congratulations, Her Excellency General Yusuf Tafida.” Dada bai motsa ba. Bai yi murmushi ba. Bai yi mamaki ba. Sai dai zuciyarsa ta furta abu guda ɗaya dai-dai da lumshewar idanunsa a hankali (Wata rana gaskiya za ta dawo da kanta. In dai har zuciya bata manta da UBANGIJI da masu gaskiyar ba) sai kuma a hankali ya ajiye Alkur'anin ya zame zuwa sujuda. Ya jima kafin ya ɗago ya sake ɗaga hannu yana ambaton, “Subahanal-lah! Allahu-akbar!”. Akan tausasan laɓɓansa Bai ce ya damu da samuwar shugabancin Janar Tafida domin ya fita anan ba, amma tabbas ya damu da addu'ar ƙasar nan tasamu mai kishin ƙasa kamar Janar da yakema ƙyaƙyƙyawan fata akowane motsinsa, ta samu shugaba mafi alkairi, yana ji kuma a ransa ogansa kuma yaya koma uba shine zaɓin ALLAHn da suke fata da roƙa in sha ALLAHU. Sake juyawa yay yana kallon tvn a karo na biyu, dan duk da sanarwar dare ce wasu wajajen har al'umma sun fara bikin murna, sauke numfashi mai nauyi yayi, zuciyarsa tana ƙonewa irin ƙonawar da MAZAN FAMA kawai ke iya fuskanta a lokacin da suke iya hango HASKEN MASU GASKIYA...... ÷÷÷÷÷÷÷÷÷÷÷÷÷÷÷÷÷÷÷÷÷÷ ★ONE WEEK LATER★ Sati guda kenan da bayyana sakamakon zaɓe. Janar da ubannin gidansa dama talakawan ƙasa da suka zaɓesa sun sha shagulgulan biki tako wane ɓangare. Idan ka cire sauran mabiya sauran jam'iyyu dake cikin takaici da baƙin cikin rashin samun nasara. Sai dai abinda mu talakawa da muke a wannan yanayin basu fahimta ba. Su waɗan can manyan da suke so tuni sun ƙulle da Janar ɗin anata farin cikin samun nasara. Sai a kafafen media ne kawai suke suka da nuna rashin jin daɗi. Duk da kuwa da yawansu har cikin zuciyarsu suna jin rashin daɗin, amma suna shanyewa saboda a hakan ma dai da ai dasu za'aci gwamnatin tunda dama duk tafiyar ɗaya ce a baɗini, a zahiri ne ake daban-daban. A lokacin da nan ake faman bidirin farin ciki ga sabon shugaban ƙasa janar Yusuf ba haka bane ba. Duk da bai kai ga tarewa a gidan Gwamnati ba aikin suke ta ƙarƙashin ƙasa shi da Daddy Imran da Haydar Galadima (Faro). Dan a yanzu haka a yau Janar Tafida ya gama ganawa da kwamitin miƙa mulki da sukai zaman meeting da tunda aka ci zaɓen nan shi suketa zamanyi saboda tsare-tsare musamman ƴan jam'iyya da kowa ke ganin lokacin fanshe wahalarsa tayi za'a bashi muƙamin da yake buƙata. Suna fitowa daga meeting ɗin aka ɗaukeshi zuwa gida. Tun ma kan ya ƙarasa shigewa falon sashensa ta baya kasancewar gidan bashi cike yake da dangi sati guda kenan ya ciro wayarsa a aljihu ya fara neman layin Daddy Imran. Bugu biyu Imran ya ɗaga, dan a lokacin shima suna tare da Faro ne a wani guesthouse ɗinsa da in har zasuyi magana akan Dada can suke zuwa. A nutse Daddy Imran yay sallama tare da gaishe da Janar. Daga nan ya amsa masa sai dai Daddy Imran baya jinsa sosai sakamakon matsalar rashin network da kowa ya sani ƙasar na fuskanta. Hakan ne yasa Janar ɗin faɗin, “Ka na ji Imran?”. “I’m here, Sir.” “Yauwa ina fatan kun kammala dukkan abinda muke buƙata?”. “Yes sir! Yanzu haka ma ina tare da Haydar anan guesthouse ɗina. Ga komai daya dace a hannunmu ko abu guda bana tunanin mun bari yayi saura. Hatta da sabbin bayanai akan Ojo Dabo ya zo da su a daren jiya, sune kawai nake ganin zanyi ƙoƙarin tabbatarwa dan nima akwai wasu a hannuna”. “Babu lokaci Imran, inaga ku ajiye sabbin bayanan Ojo yanzu a hannunku, muyi amfani da tsoffin dake wajenka zasu wadatar. Dan wannan aikin shine farko da nake son na gabatar a ƙarƙashin mulkina a ranar dana taka ƙafata a gidan gwamnati in sha ALLAHU washe gari sake nazarin shari’ar Haysam Abdul-rasheed Shehu zai tabbata. Babu wani aiki da zan gabatar na tabbatar da godiyata ga ALLAH sai in fara da wannan. Dan haka ku kasance cikin shiri kawai”. Daga can Daddy Imran ya runtse ido yana sakin wani wadataccen murmushi mai faɗi da armashi, dan yana jin kamar an buɗe wata ƙofa da ta rufe a zuciyarsa da ƙwaƙwalwa a shekaru takwas da suka gabata, ƙofar dawowa, ƙofar adalci, ƙofar fansa. Received at 6:11Cike da wata irin muryar shauƙi ya furta, “Sir! Umarninka kawai muke jira a wannan gaɓar”. Murmushi mai faɗi shima Janar ya saki, tare da faɗin, “Imran… ka shirya abinda na tambaye ka?”. “Na shirya Ranka ya daɗe. Na dawo da kowace takarda, kowace sanarwa, kwafe-kwafen shari’a, rahotanni, bincike, duk wani abu na shekaru takwas ya kammala a cikin kundi guda ɗaya. Kundin da saka hannunka kawai yake buƙata da umarni yayewar baƙin labulen daya rufe min gani da jin Zak-Shadow. KIƊA A RUWA MAI TADA HANKALIN DODONNI.” “Good Imran. Lokaci ya yi da zan sa hannu wajen dawo da gaskiya. Lokaci yayi da The two shadows zasu sake bayyana a inuwa ɗaya. Amma…” ya ɗan yi shiru, sai kuma ya cigaba da faɗin “......ba za mu je tare da kararrawa ba.” Daddy Imran ya fahimta. Aikin da aka basu ba na kan titi ba ne. Yana cikin inuwa, cikin sirri kamar yadda azzalumai ke yin wasan su. Tamkar yana a gaban Janar ya ƙame jikinsa waje guda irin aƙidar sojoji da girmamawarsu, sannan ya sara masa da Salute na girmamawa mai harsuna da yawa har Janar na iya jin ƙarar bugawar ƙafafunsu shi da Faro da shima ya miƙe ya ƙame. A tare suka furta, “Yes, Sir. I'll handle it quietly”. Daga can shima Salute ɗinsu Janar yayi yana wani shegen murmushi mai matuƙar bayyana tsantsar makamancin farin cikin da yake a cikin zuciyarsa. Daga haka ya yanke wayar. Ba ajiyeta yayi ba, sake lalubo wata number yayi. Lambobi ne da ba kowa ke da su ba, lambobin da suka tsaya tsayin shekaru biyu babu wanda ya kira shi da su. Badan bai isa ba, sai dan shiri irin na masu makirci dake da dama a hannu. Sai dai yau shi zai kira, kiran da dole a ɗauka masa kuma a risina masa, dan wannan kiran ya zama dole ga masu amsawar.. A bazata kiran tsohon Janar ya shiga wayar babban hafsan tsaro da zai hau aiki tare da shi a sabuwar gwamnatinsa. Kiran daya saka General a ƙaulani, firgici, ruɗani duk da bai san takamaiman dalilin sa ba. Amma shi ya san jiya ba yau bace, ko giyar waye yasha bai isa hana kansa amsa wannan kiran ba a yanzu. Cike da rawar jiki kuwa ya amsa, cike da girmamawa da risinawa da ƙanƙan da murya ya fara gaishe da tsohon Janar ogansa a gun aiki, sabon shugaban kasar sa mai jiran gado kuma a yanzu. Janar Yusuf Shu'aibu Tafida yay wani murmushi mai ma'anoni da yawa yana mai jinjina kai. Lallai ƙasa ta lalace, lalacewar da mutane sun koma girmama kujerun iko sama da girman daraja da kimar ɗan adamtaka da UBANGIJI yayi ma bayinsa. Bai ja tunaninsa da nisa ba ya fara magana ba daɗi, ba sirri mai nauyi, amma da umarni. “Ina bukatar sashin ku ya fara nazarin batun jami’in SOJA da aka jefa cikin gidan maza shekaru takwas da suka wuce. Ba tare da hayaniya ba.” Cikin matuƙar bugawar zuciya Genaral ya furta, “Sir! Zak-Shadow?”. “Eh. Na san akwai ɗan hazo. Ina so ku share min hanyar ganin shi cikin sirri kafin na shiga ofis.” Yawu mai matuƙar kauri Genaral ya haɗiya jininsa na tsitstsinkewa, a take zufa ta jiƙe jikinsa sharaf. Ya kasa magana har sai da Janar Yusuf yay gyaran murya irin ta manyan da umarni kawai suke badawa sau ɗaya tak. Kamar wanda aka farkar a suma General ya amsa da sauri har harshensa na sarƙewa. “Za’a yi, Ranka ya daɗe. Amma wannan… zai bugi wasu mutane.” “Ai dama so nake ya buge sun da bulala mai zafi da dafi. Dan lokaci yayi da zasu ji su kuma sani. Gaskiya ba ta tsorata da MAKIRCI ko ƘARFIN IKO. Gaskiya ce take tsoron TUGGU koda MAKIRCI yayi nasarar ƁOYETA.” General ya kaɗa kai kamar tsohon ƙadangare dan ya kasa magana ma. Sai sake wanke masa jiki zufa take dan tabbas a wannan gaɓar yana a tsaka mai wuya ne..... <<%>>★<<%>> PRISON *8:30pm* aka samu baƙuncin jami’an tsaro na musamman, dole a kirasu jami'an dana musamman, domin ko sun iso ba tare da hayaniya ba balle yanayin rububi. A nutsensu suke cikin Uniform. Kai tsaye kuma sun nema ganin shugaban prison ɗin ne ta hanyar bama securitys ɗin dake kula da shiga da fitar kowa takarda. Received at 6:11 PM [01-16, 11:37] +234 703 449 6321: KIƊA A RUWA 2 30 .........Isowarsu ɓangaren da Dada yake ya tabbatar min da lallai ba wannan jami'an bane ainahin vistors ɗin, dan a ƙofar wajen suka samu wanda akaima rakkiyar. Bayan sun ƙame tare da salute ɗinsa ɗaya ya matsa yana sanar da ogan nasu cikin magana ƙasa-ƙasa. Kansa kawai ya jinjina batare da yin magana ba, kuma ba'a ganin fuskarsa dan ya saka norse mask ga eyeglass, sannan kansa da hula p-cap data sake ɓoye ainahinsa. Yana sanye cikin ƙananun kaya daga sama har ƙasa baƙaƙe. Har cikin ainahin ɗakin ganawar securitys ɗin sukai masa rakkiya, dan shi kaɗai ya shiga banda jami'an sa. Koda suka nuna masa kujerar zama bai zauna ba, yana daga tsaye kawai a cikin dakin yana jiran shigowar wanda zuciyarsa ke bugawa saboda tsoron abin da zai gani, tsawon shekaru biyar har da wattani huɗu a kai bai ga Zak-Shadow koda daga nesa ba. Mintina kaɗan da suka kasance masu nauyi na cika wanda yake begen gani da ƙagauta ya iso. Cak numfashinsa yaso tsayawa sakamakon bayyanar mazan fama, sosai ya rame fiye da wancan ganin da yay masa na shekarun baya. Duk da lokaci-lokaci ana masa aski hakan bai hana gashin saje taruwa a farar fuskarsa ba da kansa. Fata kam tayi haske da kwanciya saboda zaman waje guda. Sai dai baza'ace akwai laushi na jin daɗi ba. Yanda yake kallonsa haka shima Dada ke kallon nasa, dan duk da ya rufe fuska a kallo ɗaya ya gane wanene, dan ko cikin rububi manta wannan halittar ta gabansa sai dai ɗimuwa a lokacin magagin mutuwa amma ba a cikin hayyaci ba. A karo na farko baƙon ya ɗan murmusa da ƙoƙarin danne abinda ke yunƙuro masa. Sai kuma ya kai hannu a hankali ya zare glasses ɗin idanunsa. A tare idanuwa nasu suka haɗu a cikin na juna. Imran ya kasa motsi. Haka shima Dadan bai motsa ba, dan kai tsaye zuciyarsa yake kallo a zahiri. Fin sakan talatin suna a haka kafin Dada ya saki wani ɗan murmushi da lumshe idanu ya buɗesu a lokaci guda, a hankali ya cigaba da takowa har inda Imran yake. Har yanzu nutsatstsiyar fuskar nan tasa da murmushin nan nashi na ƙasaita, ya motsa lips kamar mai son raɗa ya furta, “Ranka ya daɗe, soja… har yanzu baka daina kuka da ido ba?”. Kauda kai Daddy Imran yayi yana haɗiye hawayen da basu ƙaraso cikin idanunsa ba, amma da yake Zak-Shadow ɗin nasa Zak-Shadow ne shi har ya karantosu daga ƙirjinsa. Wata ƴar ƙaramar dariya Dada ya saki da kaiwa zaune, ƙafarsa ɗaya kan ɗaya hannayensa da yau babu handcuffs harɗe a ƙirjinsa ya sake faɗin, “Sit mana my Boss”. Yanzu kam shima murmushi Daddy Imran yayi, sai kuma ya gyara kujera ya zauna irin zaman Dadan suna kallon juna tamkar wani saurayi da budurwa. “Na yi missing naka sosai, Zak...” kalma mafi nauyi da girma dake riƙe da zuciyar Imran ta fito daga bakinsa. Sai kuma hawaye suka cika masa idanu. “Idan ka cigaba da wannan kukan, how many missions za ka gama?. Kalleni da ƙyau ina raye, kuma ina cikin ƙoshin lafiya mi kake buƙata bayan hakan daga UBANGIJI? Ko sai na tashi mun gwada ƙarfi ne?”. Dariya sosai Daddy Imran keyi cikin hawaye, dan ya fahimci yau raha Zak.. ɗinsa ke ji. Kai tsaye ya ce, “Kai dai ba zaka canza ba.” “Zama da kai ne Imran, kwana biyu sai nake jin matsanancin kewar ka. Ashe kana gab da ni ne shiyyasa.” “Duk randa muka zama a nesa da juna lallai ƙasa ta bizne idanun wani a cikinmu ne ko mu duka. Sai dai ni nafi fatan fara tafiya na barka dan nasan bazan iya ɗauka ba idan kai ne ka barni”. Idanu sosai Dada ya zuba masa. Dan haka shiru ya biyo baya, irin shirun nan mai cike da abubuwan da bazasu faɗu ba. Tsohon lokaci kafin Daddy Imran ya katse yanayin nasu ta hanyar miƙa masa briefcase daya shigo da ita. “New President Yusuf Tafida… ya buƙaci nazarin shari’arka tun daga farko har ƙarshe. Sai dai ba yau za mu faɗi komai ba. Amma daga yau ɗin game ya fara dawowa.” Received at 6: Cak numfashin Dada ya tsaya ba ƴan sakanni, ya kuma zuba ma Imran ido tamkar zai haɗiyo shi da su, “Sabon shugaban ƙasa, zai iya zama yana da alaƙar huɗɗa da waɗanda suka karyar da ni fa Imran, sai dai maybe shima bai sani ba.” “Miyasa kai wannan tunanin? Dama ce fa tazo mana daga UBANGIJI. Kafa san wanene Janar”. “Tabbas nasan Janar, sani na nagarta da mazantaka. Ba kuma bana farin ciki da damar bane, ina ganin kamar yazo da gaggawa ne, gaggawar da zasu iya kaishi ƙasa da ita a kaina, dan yazo musu da bazatar abinda ba shi suke hasashe ba a kansa. Dole ya zama mai zaɓi biyu a lokacin da ya bayyana musu ainahin fuskarsa a kaina. Saboda a tsarinsu babu wani shugaban ƙasa da zai kasance baya abota da su. Koda sun ɓoye masa waccan fuskar tasu a yanzu inada tabbacin zasu bayyana masa ita ya sansu ya san aikinsu. Matsalar kuma idan har yana son gaskiya, to sai ya tabbatar min da hakan da aikin shi. Ba da kalamai ba. Dan kar ya kasance na amince na fita ya zama yana cikinsu bazan ƙyalesa ba koda shine Abdul-rasheed Shehu Isa Kobi”. Daddy Imran ya fahimci hangen Dada, dan haka ya sauke numfashi mai nauyi yana jinjina kansa da faɗin, “Haysam na yarda da ku kai da Janar da Faro. In sha ALLAHU Janar bazai bamu kunya ba, yanda muka fara da shi zamu ƙare a tare koda sai bayan babu ran mu ne NASARA zata bayyana. Na tabbatar shima kamar mu ya ke, idan gaskiya tana gona, zai haƙo ƙasa ya nemota da kansa.” Dada yayi murmushin mai zafi fiye da bala’in da yake hangowa da ƙurar da zata tashi. “Shike nan Imran! ka gaya masa, idan yana neman gaskiya, kada ya zo da haske. Duk wanda yake neman ƙasar nan, sai dai ya biyo duhun dare. Ni zan fara jiranku daga yau. Ku dinga tuna kuma zan dawo da gudunmawata. Game on.... again.” yay furucin ƙarshe da wani salo yana kashema Imran ido ɗaya da yin alamar harba bindiga da yatsu biyu. Dariya Imran ya kece da ita, irin dariyar da shi kansa yasan ya jima baiyi ta ba. Kai koda kwatance baya kawota a zuciyarsa balle ma fuskarsa. Shima Dadan kallonsa yake yana wani shegen murmushi mai bayyana haƙwara, kai daka gansu kasan ƙara'in farin ciki ne na tsahon shekaru ke fidda kansa tun daga ƙasan zuciya har zuwa fuskokinsu. Sai dai Imran yasan minene ma'anar murmushi irin wannan a fuskar Zak-Shadow ɗinsa. Ya tabbatar zafin daya jure cikin wannan duhu na tsawon shekaru takwas da wata huɗu, sakamakon wannan murmushin idan ya fito ƙasa za ta sake girgiza...... <%><%><%><%> “Malam Almu maganar ciwo ai ta wuce wasa, kuma ta kori komai a rayuwa. Dan haka babu batun neman alfarma zuwa gida daga garemu. Ka shirya kawai abinka ga kuɗin mota. Wannan kuma sai kai amfani da shi wajen kaita asibiti, ALLAH ya bata lafiya yasa kaffara ne. Zaka wuce yau ne ko sai zuwa gobe? Dan muma zamuje airport ne ɗaukar Bilal yau zai dawo”. “Kai kai Masha ALLAH. Yau Alhaji Bilal zai dawo ashe? To bari na jira ya dawo tukkuna ai kamar zai fi”. Kai tsaye Mammah dake saurarensu ta ce “A'a Malama Almu ban goya bayan haka ba, kaje dai tunda zaka dawo ai. Itama Innarka na buƙatar ka, kuma tana buƙatar a kaita asibiti. Ina ga ma idan kaga jikin babu daɗi sosai kawai ka ɗakkota zuwa goben ku taho nan a kaita asibiti zai fi”. Godiya maigadi yake jerama Mammah dasu Yaya Ja'afar har hawaye na cika masa idanu. Yana tausayi da mamakin alkairan bayin ALLAHn nan, shiyyasa a lokuta da dama idan ya tuna dalilinsa na zaman gidan nan tare da su sai yaji zuciyarsa na karaya akan ƙudirinsa. Haka ya miƙe yana shartar hawayen da shi kaɗai yasan dalilinsu ya fita... A gurguje maigadi ya shirya tare da damƙa gate a hannun sabon driver kamar yanda su Ja'afar suka ce masa. Ya wuce ya tafi yana ayyana wa a ransa ai bazai wuce jibi ba, idan har zuwa kwana uku bai dawo ba to bazai wuce safiyar kwana na huɗu ba in sha ALLAHU. Dan babu wani ciwo da Innarsa keyi kamar yanda ya faɗa, ogansa ne ya bashi umarnin zuwa ya sameshi da gaggawa a yau. Received at 6:11Saboda shi Innarsa ma ta jima da rasuwa, a hannun kishiyar uwa ya tashi, azabar data bashi da wahala ta maida shi yanda yake a yau, sai dai a gidan Mammah sanin mutum cikakke sukai masa mai nagarta sakamakon ɓoye ainahin wanene shi da yayi a garesu.... Tofa, wata sabuwa maigadi🤔🤐🏃🏼‍♀️. ÷÷÷÷÷÷÷÷÷÷÷÷÷÷ ★DUBAI★ Duk yanda su Hajiya Hasiba suka so tafiya India bincike akan Adeel bai yiwu ba. Dan kuwa randa ta samesa da dabarun zuwa India business a ranar yace mata ya kammala shirin tafiyarsu. Ta jira har su dawo sai taje. Kota sanar masa business ɗin da kamfanin da zasuyi koma miye a kawo mata shi. Jin haka yasa ta saurin cewa ba damuwa suje ɗin kawai su dawo tayi nata uzirin daga bayan. Shirin nashi bai bata tsoro ba sai da ya tabbatar mata harda su Nabeeha za'a. Ta tambayesa ba'asi yace hankalinsa zaifi kwanciya idan tana acan tare da shi. Dan karma ya barta anan wani abu ya faru. Duk da kuwa yana da ƙarfin ikon sakawa a bibiyar masa ita duk inda ta shiga a cikin ƙasar. Amma baya buƙatar hakan, dan bayan abokinsa ɗaya jal babu wanda yasan yana bibiya ko son auren Nabeeha. Abinka da sai yanda akai da kai, dole suka hau shirin tahowa. Sai dai ran Nabeeha da Ismat fal farin ciki. Hakama Mamawo, dan koba komai itama akwai nata shirin data barma tata zuciyar game da Adeel ɗin, tana ganin kuma zuwansu ƙasar tasu ce zai iya cika cikin sauƙi saɓanin anan da wasu dalilai zasu iya hanata. Amima da Raihana ko basu so wannan tafiya ba. Dan harga ALLAH su daɗin zaman Dubai suke ji, har basa son tuna zuwa ƙasar haihuwarsu. Shiyyasa ma suke matuƙar jin haushin Nabeeha da taƙi bada haɗin kai bori ya hau. Dan wlhy da a cikinsu Adeel ya nuna yana son wata hohoho da wani labarin ake ba wannan ba ma..........✍️ Received at[01-16, 11:37] +234 703 449 6321: 31 ........Sun iso cikin dare. Kasancewar a babban birnin suka sauka yay bucking hamshaƙin hotel na gani na faɗa da yafi kowane hotel tsari da ƙayatarwa. Su kuwa gidan Hajiya Hasiba suka sauka. Dan tun a can ya nuna musu baya son asan tafiyarsu ɗaya da shi har ya kammala aikin nasa su koma.             Ba laifi gidan babba ne sai dai ba ƙato ba. Six bedrooms ne. Sai faluka guda uku. Akwai na baƙi da bedroom ɗaya, sai falon ƙasa shima da bedrooms 2, sai upstairs da falo da 3 bedrooms shi kuma. Akwai kitchen a ƙasa. Sai can gate akwai ɗakin maigadi. Shi kaɗaine kuma a gidan da matarsa da yaransu biyu. Kasancewar idan suna nan itace ke musu aiki. Dan haka tun suna can ta sanarma maigadin zuwansu. Haka matar ta yini yau tana ƙalƙale gidan, da yamma mai musu abinci tazo tai musu, sai da ta shirya komai a dinning sannan ta wuce dan dama ba'a nan take kwana ba.        Tun kan Hajiya Hasiba ta shiga siyasa tana da kuɗi, dan kuwa tako wace hanya nemansu akeyi. Alaƙarta da manyan ƙasar musamman first lady ya sake armasa dukiyarta da sanin manyan mutane da ake harkokin da basai ance komai ba (🥱🤭🤫), ko wannan gidan ƙyautarsa aka bata sukutum kamar juye alalar gwangwani a plate 🥱🤣. A yanzu kuma ga Adeel ya ida jiƙeta.          Duk da ba wata gajiya ce a tare da su ba kowa sai wayyo-wayyo yake yi. Duk suka zube a falon ƙasa suna sauke numfashi, maigadi da matarsa nata kai-kawon shiga musu da kaya da jera musu sannu. Da ƙyar suka iya tashi bayan wani lokaci suka haye sama su duka. Dan duk can suke da ɗakunan barci har Mamawo ɗin ma daba wani zama take sosai a ƙasar ba. Wanka suka fara gabatarwa sannan suka nema abinci. Suna kammala ci kowa ya nema makwanci. Basu tashi farkawa ba a washe garin ma sai ƙarfe kusan sha biyu. Haka sukai wanka suka sakko ƙasa neman abinci. Sunko samu Joy ta kammala komai har na rana, aiko suka far masa da ci sai da kowa yay ƙat.       Wajen ƙarfe uku Nabeeha tace tana son zuwa gidanta ɗakko wani abu. Aiko daga Mamawo har Momyn tasu suka hayayyaƙo mata da masifa. Da farko shiru tai musu, sai daga baya ta saka musu kuka. Jikinsu ne kuma yay sanyi, dan haka Momyn tata tace ta shirya amma su Ismat ne zasu rakata su dawo tare, amma yau yamma tayi ta bari sai gobe. Bata musa ba tace ta yarda....... <<%>><<%>><<%>>            Kamar kullum yau ma a dai-dai lokacin da aka saba tashinsu islamiyya aka tashe su. Kasancewar Yaya Mu'azz ne ya kawosu sun tabbatar bazai zauna zaman jiransu ba kamar driver har zuwa yanzu. Sai dai zai dawo ya ɗauke su. Su duka zukatansu cike suke da zumuɗin komawa gida saboda Uncle Bilal, dan ba ƙaramar kewarsa sukai a watannin nan da baya nan ba. Sune farko fitowa a aji, ajin nasu kuwa daga shi sai na ƴan sauka, duk da suma dai gab suke da kaiwa sittin ɗin in sha ALLAHU.      Hayaniyar dake tashi a ajin ƴan saukar ne ya daki kunnuwan su Nimrah da suka fara fitowa, kallon juna sukai ita da Ruky, sai kuma suka nufi ajin da sauri dan ganewa idanunsu abinda ke faruwa. Gaba ɗaya ajin ya hargitse da ɗaliban ƴammata da samarin cikinsa, dan kuwa sun girmi su Nimrah su zasu iya kaiwa sha bakwai ne. Yanda suka dunƙule waje guda suna jefe-jefen takalmansu yasa Nimrah data kutso kai cikinsu kallon abinda suke jifar. Abin takaici abin mamaki ba komai bane sai mage. Wata baƙar mage ce da jariran ƴaƴanta biyu, ɗaya fari tas ɗaya baƙi da kwalliyar golden a jikinsa. Mai kwalliyar golden ɗin na kwance kansa da jini alamar wani ne ya jefesa, farin kuwa ya maƙale jikin uwar da itama har an jimata ciwo sai wani irin nishin kuka take. Ai bama tasan ta zabura inda magen take ba jikinta na rawa.        Ihu ƴan ajin suka fara mata da kiran karta je ba mage bace aljana ce ko wata mayyar ta rikiɗa tunda ance mayu na zama mage, amma kota kansu batabi ba ta ƙarasa. Hannu ta saka ta ɗauki magen ta rungume, tare da ɗaukar farar itama dake jaririya abin sha'awa, tana kai hannu zata taɓa golden ɗin dake kwance a ƙasa kawai cikin ƴan ajin wani ya wulwulo dutsina har biyu. Ai ko ɗayan ya sauka akan magen babba ɗaya akan Nimrah. Received at     Juyowa Imam yay yana hararar Ruky da tai maganar. Kafin yace wani abu cikin sake lanjarewa Nimrah ta ce, “Dan ALLAH Yaya. ALLAH su Afry ma naso ko?”. Ta juya tana kallon su Aheel. Magiya suma suka fara. Sai lokacin Mu'azz daya ɗan juyo ya hararesu ya sake maida kansa ga titi sannan yay magana. “Ku yaran nan kun cika nemarwa mutane hanyar kashe kuɗi. Ga asarar salla a jam'i da kuka jawo mana. Wai kun manta yau Uncle Bilal zai dawo ne”     Su dai basu kula faɗansa ba suka cigaba da maguyarsu duk da ransu cike yake da farin cikin batun dawowar Uncle Bilal da zaiyi a daren nan. Sai da yay ƙwafa sannan ya rage gudun motar. Canja hanya yay zuwa inda yasan ana saya musu ice-cream ɗin da suke so. Basu wani jima ba suka iso. Har zasu fito ya hararesu yana faɗin, “Ina zaku bimu da uniform a jiki ace satoku mukayi, ke kuma ga rauni a kai”.       “Abinda ba'a ganin ciwon na rufe da hijjab. Dan ALLAH ka barmu muje”. Nimrah ce mai maganar cikin tura baki. Mu'azz zai ƙara magana Imam ya ce, “Barsu dan ALLAH Bro. Muje, muna sake tauye lokacin salla ne kawai a wannan surutun”.     Ba yanda Mu'azz ya iya yayi gaba suka bishi, Ruky harda masa gwalo. Su Imam na gaba riƙe da hannayen su Abees, su kuma suna biye da su, suna gab da shigewa Ruky ta riƙe hannun Nimrah ta tsayar da ita, batare da tayi magana ba takai hannu tana gyara mata hijjab ɗinta ganin bandage ɗin kanta ya fito. Hakan yasa suka rigasu shigewa. Dai-dai suma suna ƙoƙarin shigewa suna gulmar su Mu'azz ɗin ƙasa-ƙasa suka kusa cin karo da mutanen dake ƙoƙarin fitowa. Da sauri Ruky tai baya tana jan hannun Nimrah, sai dai cikin rashin sa'a ta tafi zata faɗi, a cikin waɗan can ɗin ɗaya yakai hannu zai riƙota.      Cike da tsiwa ta ce, “Malam miye haka, karka taɓani”.      Duk da da hausa tayi, bai ji mita faɗa ɗin ba saboda ba yarensa bane yanda sautin muryarta mai cike da tsiwa ta daki kunnensa sai ya tsaya cak, tare da ɗago manyan idanunsa ya kalleta. Sai akai sa'a kuwa dai-dai itama ta balla masa harara...........✍️ Received at 8:16 PM [01-16, 11:37] +234 703 449 6321: 32 .........Ba ƙaramin motsawa zuciyar Adeel tayi ba, batare da ya shirya ba ya saki murmurshi mai faɗi yana ƙare mata kallo. Sake balla masa harara Nimrah tayi tana bin Ruky dake jan hannunta sukai ciki.         Yako lumshe idanu ya sake buɗewa a kansu. Zai iya rantsuwa tunda yake bai taɓa ganin baƙar fatar data gama tafiya da duniyarsa lokaci guda irin yarinyar nan ba. Gata dai ba wata ƙatuwar budurwa ba, hasalima a ƙasarsu bata wuce babyn raino ba, amma tayi masifar tafiya da dukkan zuciyarsa. Abin mamaki kuma ba irin son da yake jin yanama matan baya bane na sha'awa, wannan wani baƙon al'amari ne mai girman gaske a gareshi da ban mamaki...        “Oga ya dai?”.    Wanda suke tare ya faɗa yana taɓa shi. Juyowa yay ya kallesa, sai kuma ya ɗan sake murmusawa da faɗin, “Mi ta faɗa ɗazun?”.       Murmurshi wacan ɗin yayi, duk da bai san wanene Adeel ba a matsayi na rayuwa balle ma ƙasar da ya fito. Dan kuwa daga hotel ɗin daya sauka ne ya buƙaci ɗan rakiya zaga gari shine aka bashi ma'aikacinsu ɗaya da mota, har sun wuce wajen nan ya ɗauki hankalinsa yace su shigo dan ya ga harda kilishi ake saidawa. Cikin harshen turanci ya sanar masa abinda Nimrah ta faɗa. Kawai sai ya sanya dariya. A ransa yana raya (Wato ita tana jinta wata mace ce karna taɓa ta). A zahiri kam waje ya ƙarasa fita, sai dai ya tsaya a jikin motar su ne ya zubama hanyar shiga da fitar idanunsa....        Babu jimawa kuwa su Nimrah suka fito su Mu'azz biye da su. A gaban idanunsu duk suka shiga mota, sai da yaga Imam daya amsa tuƙin yanzu ya tada mota sannan shima ya shiga tasu yana faɗama abokin tafiyar tasa su bisu. Bai kuwa musa ba tunda aikin kuɗi yake. Haka ya dinga binsu a baya ta yanda bazasu gane ba har gida. Daga can ɗan nesa kaɗan suka dakata, har motar ta shige aka maida gate ɗin aka rufe.         Kai tsaye Adeel ya ce, “Ya sunan Street ɗin? Sannan kasan gidan waye?”.      Kai ma'aikacin hotel ɗin ya girgiza masa da faɗin, “Ban san gidan waye ba gaskiya. Amma sunan nan ɗin KOBI STREET.”      Sunan Kobi Street ɗin ya maimaita da karyayyen harshensa, kafin yace, “Okay zaka iya sake kawoni gobe?”.        “In sha ALLAHU Sir!”.      Fuskarsa da murmushi yace, “Muje inda zan samu layin ƙasar nan da waya”.      “Okay Sir”.    Daga haka suka bar wajen.  ____       A cikin gida kuwa tunda su Nimrah suka fito a mota sabon driver malam Buba dake tsare da gate a yau ya zuba mata ido. Duk yanda yaso daurewa sai ya kasa, sai da ya iso inda suke yana tambayar lafiya kuwa yaga bandeji a goshin Nimrah ɗin. Imam ne ya bashi amsa a taƙaice da cewar “Ciwo taji a islamiyya”. Itako da tunda tai masa kallo ɗaya tsigar jikin nata ta fara tashi ta kauda kanta. A taƙaice ta gaisheshi kamar kowa sukai gaba ita da Ruky. Haka ya bisu da kallo yana jin kamar ya bisu ciki. Sai dai ya danne zuciyarsa da ƙar, amma can ƙasan rai ayyanawa yake (Lokaci yayi da zai fitoma Nimrah ɗin a mutum tasan shi ɗin waye).      A ciki ma hankalin Mammah da su Aunty Shariffa ba ƙaramin tashi yayi ba. Dan su Yaya Ja'afar sun tafi Airport ɗaukar Yaya Bilal dake gab da sauka, tuni sun cire mata hijjab suna duba wajen. Sai ita ke magana cikin shagwaɓa da son kwantar musu da hankali tana faɗin, “Babu fa zafi. Tunda aka min allura ya daina ciwo”.       Faɗa Aunty Biebah ta fara akan cewa bazasu yarda ba, gobe sai taje islamiyyar da kanta dole yaron nan a hukunta shi. Sai da Mammah tai maganar “Baza'a kai ga nan ba. Tunda ance kuskure ne to a barshi a hakan ALLAH ya kiyaye gaba.”     Badan sun so ba suka haƙuran. Amma Mu'azz dama ya ayyana a ransa sai yaci uban yaron tunda shima islamiyyar yay sauka, yanzu kuma weekend kawai suke zuwa Tahafiz shi da Aunty Biebahn. Ɗaki suka wuce yin salla. Mammah tace Biebah ta bisu tasa towel a ruwan zafi ta gasa mata goshin da fuskarta. Da to ta amsa tana bin bayan nasu... <<<<<<<。⁠◕⁠‿⁠◕⁠。>>>>>>>       ★RANTSUWA★ Received at 8:16     A yau sati uku da fadar da tabbatar da Janar matsayin shugaban ƙasa ta cika, a yau kuma ake shirye-shiryen rantsar da shi da shiga gidan gwamnati da aka kammala gyarawa tsaf. Tuni a cikin sati ukun nan ya kammala komai akan fiddo Dada, office kawai yake fatan shiga ya zartar da hukunci. Yanda kuma suke komai a sirrance daga shi sai Imran, da Haydar yasa zai mamayi mutane da yawa akan wannan kyakkyawan ƙudiri nasa.        Kamar yanda aka tsara an gabatar da rantsuwa tako wane fanni a ƙasar, sabbin shugabanni da wanda suka sake komawa tenure ta biyu duk sun shiga gidan gwamnati a wannan rana ta litinin tare da sabbin ofisoshin su. Sai dai mu cigaba da musu fatan alkairi da nasarar yin adalci ba satar kuɗaɗenmu ba😝🏃🏼‍♀️.      (Mai son soyayya da ɗan shugaban ƙasa tamun magana mu sasanta ta biya cin hanci na haɗasu🥱💃. In baki da ko sisi karma kizo😏🙄🤭🏃🏼‍♀️.)        ★A yau daren farko na sabon shugaban ƙasa Janar Yusuf Shu'aibu Tafida cikin gidan gwamnati. Tsaye yake cikin ƙayataccen falon daya kasance na ƙarshe sai bedroom ɗin barcinsa, tunda ya shigo gida bisa rakkiya bai buƙaci ganin ko ɗaya daga iyalansa ba, sakamakon son fara zartar da babban birinsa. Komai kashe yake a falon in ka cire ac kawai shima ba'a wani sakashi da ƙarfi ba, an sauƙaƙa hasken fitilu gaba ɗaya dan falon na cikin ɗan duhu-duhu, zaune yake shi kaɗai kamar yanda yafi buƙata, tunaninsa gaba ɗaya ya tsaya ne akan mutum guda ɗaya, mutumin da yake ma kallo mafi muhimmanci na farko da zai shimfiɗa wannan mulkin mai cike da cakwakiya da ƙalubale kashi-kashi da shi, dan tun a yau ɗaya da fara shigarsa office ya fahimci hakan. Saboda haka bazaiyi ƙasa a gwiwa ba ko sakaci, yana buƙatar Haysam Abdul-rasheed Shehu a cikin wannan tafiyar tasa tamkar yanda ƴan ƙasa ke buƙatarsa koda basu san muhimmancin sa a garesu ba.         Ƴar ƙarar buguwar agogon dake bango falon ya katse tunaninsa, numfashi ya sauke a hankali, dan ƙarar ta bugane tamkar da bugawar umarnin zuciyarsa dake ambaton (lokaci ya cika, ka fitar da takardar zartarwa kawai, rikicin da kake kallo da ƙalubalen bai fi nauyin burin nan naka ɗaya ba, cikashi tun a wannan daren masalaha ce ta zuciya da kwanciyar hankali ka, fitar Zak-Shadow daga dunkulallen makircin da aka garkame shi cikin kurkuku tsawon shekaru takwas itace zai tabbatar ma masu shirin mamayeka kai ba kurar wasansu bane, aiki kazo yi ga ƙasa da al'ummar ƙasa ba aikin aljihunansu ba).        Cike da gamsuwar shawarar zuciyarsa ya sauke numfashi, cikin nutsuwa ya ɗauki wani file da takarda a cikinsa mai tambarin ofishin shugaban ƙasa (Presidential Seal). Wannan shi ne takardar ikon afuwa da zai miƙa wa Ministan Tsaro, wanda zai tafi kai tsaye zuwa hannun Babban Hafsan Rundunar Sojin Ƙasa. Duk da yasan aikin bamai sauƙi bane a garesu; dan akwai al’amuran cikin gida da ya sani zasu taso, munafukan dake da hannu akan lamarin Haysam, waɗanda ba a san ainihinsu ba har yanzu, amma yasan zasu bayyana ne da wuri akan wannan fitar ta Haysam, dan dole suna da tasiri a cikin gwamnati harda tasa kamar yanda Haysam ɗin ya faɗa. Shi kansa daya samu wannan mulkin cikin sauƙi duk da yasan komai hukuncine daga UBANGIJIN, amma sanin wacece wannan ƙasar tasu akwai tambayoyi a ransa: Su wanene ainihi? Kuma me yasa Zak-Shadow ya zama barazanar da suka ƙuduri aniyar kawar da ita? Miyasa kowa Haysam dai Haysam dai?.         (Fitar tasa ce zata baka hasken samun wannan amsar) Zuciyarsa ta ayyana masa. Murmurshi ya saki mai ƙayatarwa cike da gamsuwa ya ɗauki wayarsa dake gefe. Kai tsaye number Imran yay kira.....         ★A yau gaba ɗaya Imran ya kasa barin office har zuwa wannan lokacin, zaman jiran kiran mutum ɗaya tak yake, kuma bazai ƙosa da wannan jiran ba daga nan har wayewar gari in sha ALLAHU. A dai-dai wannan lokacin da Shugaban kasa ke neman layinsa yana tsaye jikin windown ofishin sa yana kallon titin da ke cike da motocin jami’an tsaro. Rabonsa da cikakken barci tun dare shekaran jiya, gaba ɗaya barci ya gushe masa a cikin idanu tun bayan samun saƙon shugaban ƙasa ta text message bayan kammala rantsuwa. Received at 8:16 PMDan haka ya ƙare wannan yinin gaba ɗaya da ƙagautar jira, jiran kiran Janar da a yanzu ya shigo wayar tasa a bazata. Jikinsa har tsuma yake wajen kai hannu ya ɗaga.          “Assalamu alaikum Your Excellency…” ya faɗa cikin ladabi da kuma farin ciki da bai iya ɓoyewa ba.     Janar daya fahimci ƙagautar Imran a bayyane ya saki murmurshi, batare da jan rai ba ya furta “Imran, lokaci yayi. Takardar afuwa ta kammala.” Ya ɗan yi shiru, irin shiru mai nauyin tasiri, kafin ya cigaba da faɗin, “Ina so ka shirya tawaga mai tsabta. Ba na son hayaniya, ba na son labari ya fito. Ka tabbatar da babu wanda idonsa ke buɗe a kanku”.      Da wata irin sauke ajiyar zuciya mai masifar nauyi Imran ya lumshe ido cikin jin daɗin kalmar da ya dade yana jira kamar mafarki. Muryarsa na rawa ya furta, “Za’a yi sir. Da izinin ALLAH Zak-Shadow zai fito gobe ƙarfe tara na safe.”      “Good. Kai nake son ka jagoranta Imran. Na san kai kaɗai zaka iya tsallake duk wata inuwa daga ƙalubalensu. Zaku wuce inda na tanada dan duba lafiyarsa da saituwar al'amarinsa. Ka tsare shi da ranki. Har sai ya koma randa zai dawo ƙasa ya zama barazana, dan Zak-Shadow nake son a gani ba firsinan shekara takwas ba”.        Daddy Imran ya murmusa, murmushin jarumi wanda ya dace da mai ɗauke da nauyi mai girma na tsakanin soja da dangi. Sai da ya ƙame tare da salute sannan ya furta, “Na rantse da ALLAH za’a yi fiye da umarninka Sir. Ba zan bari koda iska tai barazanar kaɗa nauyin daya rage masa ba kafin ka gan shi duniya ta ganshi zuri'armu su ganshi.”        “I'm proud of you, Soldier”.      “Thank you, Sir. I'm proud of you too”...      Daga haka suka katse kiran, amma zuciyar Imran kamar zatayi tsallen kwaɗon sojoji dan farin ciki. Sai da yay sujidar shukur sannan ya miƙe bakinsa ya kasa rufuwa dan murmushi, ji yake kamar UBANGIJI ya sauke masa wani babban nauyi daya toshe bugun zuciyarsa a tsawon shekaru. Wayar ya ɗauka ya tura sako ga ɗaya daga manyan abokan amana da zai jagoranci motar sirri zuwa prison wato Haydar Galadima (Faro)........✍️ Received at 8:16 PM[01-16, 11:37] +234 703 449 6321: 33 ..........Fuskar former First Lady ɗauke da murmushin ƙasaita take kallon Hajiya Hasiba, sai kuma ta girgiza kai da faɗin, “Hummm.. Adeel! Adeel. Yanzu kina nufin tare da shi kuka zo ƙasar nan?”.      “Sosai kuwa ranki ya daɗe. Dan yanzu haka ma yana masauki. Kuma abinda na sanar miki ya ambata ne ya kawo shi, wato kashe Haysam. Sai dai bamu san ta wace hanya zaibi ya tabbatar ba”.       “Yana da daman bin kowace hanya, dan yana da ƙarfin ikon dukiya da sunan zuri'ar gidansu. Sai dai abinda ke ban mamaki wace manufa yake da ita akan Nabeeha har haka? Dan nasan Adeel matuƙar sani, nasan al'amarinsa akan mata. Tabbas idan yana a giyar kwaɗayin tarayya da mace komai yana iya aikatawa, da zarar ya cika burinsa kuma shike nan.”        “Amma yana iƙirarin auren Nabeeha zai yi ai. Shiyyasa ma ya iya juriyar shekaru kusan tara kenan a kanta.”       Murmurshi mai haɗe da ƴar dariya First Lady tayi. “Bazan ce miki ƙarya yake kai tsaye ba Hajiya Hasiba, sai dai zan iya miki yaƙinin ba haka bane ainahin abinda ke ransa. Duk wannan iskancin da kike ganin Adeel nayi yana matuƙar tsoro da bin dokokin ahalinsa. Ba Nabeeha ba, ko ƴar shugaban ƙasar wannan ƙasar tamu zuri'arsa bazasu bari ya aura ba. Maybe da a yankin turawa ne su barshi yay hakan, dan sunfi ɗaukarsu da kima da daraja fiye da al'ummar yankin Afirika da suke amsa sunan baƙaƙen fata. Mu a wajensu bayi ne kawai, bayin da zasu musu bauta a gidaje da masana'antu, sannan bayin da zasu gusar da kishirwarsu cike da wulaƙantarwa da izgili. Ƙalilan ne a cikinsu masu mana kallon mutane, bari na miki ƙaramin misali mana, Kinga dai ance musulmi ɗan uwan musulmi ne, amma ko a saudia idan kinje ibada baki taɓa lura da yanda in kika haɗa sahun salla da mai jan kunne ke ƙoƙarin hana gangar jikinsa raɓar taki ba?”.         “Tabbas nasha ganin hakan ranki ya daɗe”.     “Good. Idan har basu so baƙin fata a sahun bautama UBANGIJIN daya tabbatar musu su da mu babu banbanci ba sai wanda yaji tsoronsa ta yaya zasu zo mu a haɗaka ta mu'amula mai girma irin wannan? Dan haka zan sake tabbatar miki ƙarya Adeel yake yana da manufa akan bibiyar Nabeeha, akwai burin da yake son cimmawa kuma bana jin na sha'awa ne”.           “Innalillahi wa-inna ilaihiraji'un kai biri yayi kama da mutum gaskiya. Bazan ɓoye miki ba kullum cikin yima kaina irin tambayar nan nake. Sai dai ganin yanda take masa rashin kunya da nuna halin ko'in kula balle nuna jin haushi kan shafe min tantama ta. Yanzu ranki ya daɗe minene mafita? Kin san mutumin nan nada ƙarfi, kota wace hanya zaibi dan cimma manufarsa a kammu”.      “Tabbas zai bi, dan shafe babin rayuwar ɗan adam ƙaramin aiki ne daga tarin ƙananun ayyukansa. Sannan kunyi gangancin sanar masa mijin Nabeeha na rufe ne, duk da nasan idan yaso sanin hakan zai yi koda bata hanyar ku ba. Yanzu kije gida ki bani lokaci zanyi tunani, abinda na yanke zan kiraki mu haɗu ko nazo gidan na sameki, shima kuma zan je har masaukin nashi duk da banda isasshen lokaci, saboda gobe zamuje gidan gwamnati domin ganawa da sabuwar First Lady. Kin san ɗan takarar CSP candidate ɗin Excellancy ne. Dama nayi niyyar nemoki a satin nan kizo ƙasar saboda rantsuwa da akai, sai kuma gaki ALLAH ya kawo ki ma duk da an riga an gama dai”.        “Ranki ya daɗe duk abinda kuke so zamuyi, ni dai a taimaka na fara maganin wannan matsalar dan samun nutsuwa”.      “Karki damu Hasiba. Idan ta kama Excellancy ya shiga wannan maganar zai shiga. Zan saka ya nema Adeel da kansa koya gayyato shi nan gidan idan ALLAH ya ɗaura mu akansa dan abune mai wahala yazo ɗin. Amma zamu gwada sa'ar mu”.           “Nagode sosai ranki ya daɗe. ALLAH ya bar zuminci. Ya tabbatar da nasarar ku daga nan har ƙarshen rayuwa”.      “To amin Hasiba”. ✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨       ★★..10/9/2021..★★            🔥8:55 AM🔥      Duk da kasancewar hantsi ya ɗaga kurkukun ya yi shiru yau fiye da kowanne rana. Tun 8 aka kammala basu abincin safe kamar yanda komai yake a tsari aka saka kowa komawa ciki saboda baƙin sirri da zasu shigo. Sai irin su Dada da ba'a bari su fito sai da ƙwaƙwƙwaran dalili dan haka kai musu akeyi su har ɗakunansu. Received at 12:27        A bakin ƙofar gate 8:55am motocin sojoji ne masu duhun glass guda biyu suka tsaya kamar taurari a cikin duhun dare. A motar farko kawai aka sauke gilashi ƙasa tare da miƙama securitys ɗin ƙofar takarda. Suna duba abinda ke ciki suka ƙame jikinsu tare da salute ɗin motocin. Kafin da hanzari a wangale musu ƙofar suka shige a jere. Basu tsaya ko'ina ba sai a ƙofar sashen da Dada yake. Inda shugaban prison ɗin da kansa ke tsaye tare da jami'an soji na gidan guda uku alamar jiransu suke dama.        Sai da sojojin ɗayar motar suka gama fitowa da hanzari suka zagaye wajen kafin a buɗe ta ƙarshen. Col. Imran Abbas ne a ciki, cikin farin kaya na musamman bana soja ba, sai Brig. Haydar Usman Galadima (Faro). Cikin nutsuwar girma irin na masu kamewa suka fito a hankali, a take sojojin da suke tare da su harda na cikin prison dake tare da shugaban su suka ƙame tare da sara musu.      Suna ajiye hannu shugaban prison ya ƙaraso shima gabansu, ƙame jiki yay shima tare da salute nasu irin na girmamawa, suma sai suka ƙame ɗin sukai salute ɗinsa na girmamawa. Hakan na nufin kowa ya girmama girman kowanne, dan su duka ukun kowanne nada matsayin girmama ɗan uwansa a dokance. A karo na biyu sukai musabaha, kowanne fuska da murmushin mutunta juna. Kafin Colonel Imran Abbas ya miƙa takardar Presidential Pardon ga shugaban prison.       Sai da ya ƙame a karo na biyu yay salute ɗin Imran sannan ya amsa takardar. Shima sai Imran ɗin ya sake salute nashi a karo na biyu idanuwansa sun yi kaifi tamkar yana hango duk wani inuwa da zata takura masa a cikin idanun shugaban prison, sai dai babu dama, babu dalilin bijirewa.        A karo na farko, kai tsaye Brig. Haydar Usman Galadima ya furta, “Muna so a fito mana da Lieutenant Colonel Haysam Abdul-rasheed Shehu yanzu.”       Duk da shugaban prison yasan abinda ya kawosu kenan sai da numfashinsa ya tsaya cak na wucin gadi, jikinsa yay wani yamm kamar an jefasa da dusar kankara. Amma bashi da zaɓin daya wuce bin umarni na zahiri da gaskiya. Gudun kada yaransa dake zagaye da shi, da yake da tabbacin akwai idanun ɓoyayyun mutanen da suka kawosa wannan gidan suka ɗora a wannan kujerar yasa ya ɗanyi jarumtar son cizawa. Murya a takure ya furta,       “Sir… zuwa yanzu babu wani…”    Cikin zafi Imran daya gama fahimtarsa ya katsesa da faɗin, “Shi kawai muke buƙata a gabanmu. Wannan umarnin shugaban ƙasa ne. Ko akwai wani daga cikinku da zai ce bai san ma’anar wannan tambarin ba?”.         “I'm sorry, Sir!”.      Shugaban prison ya faɗa yana ƙara ƙamewa. Kafin ya juya yayma yaransa umarni da idanu. Duk da mamaki na neman kashe da yawansu saboda fahimtar abinda ke shirin faruwa basu da zaɓin daya wuce bin umarnin suma. Dole da sauri suka shige domin zartar da abinda aka saka su.....        ★A dai-dai lokacin da suke ƙoƙarin buɗe ƙofar ɗakin, Dada na zaune ne ya idar da sallar walha yana karatun Alqur'ani. Motsin buɗe ƙofar da shigowarsu bai saka ya dakata ba balle kallonsu. Dan haka suma suka tsaya tsamm alamar jira. Sai da ya kwashe mintina biyar cir da shigowar tasu sannan ya rufe Alkur'anin yana mai ɗagowa ya kallesu. A tare suka nuna girmamawar soja, kafin suyi gaisuwa da sanar masa umarnin da aka basu.      Maimakon amsawa idanu ya lumshe a hankali, sai kuma ya kife zuwa sujuda. Minti biyu cir kafin ya ɗago. Ya ɗauki Alkur'anin sa ya maida inda yake. Sai kuma a dai-dai nan jami'ai  biyu dake tare da su Imran suka shigo. Suma sunyi gaisuwar sannan suka fara tattara kayansa na buƙata masu muhimmanci. Komai baice ba, sai bin ɗakin da yay da kallo, kallo irin na bankwana da tuna abinda ya shuɗe, kafin ya juya a hankali ya nufi ƙofa jami'an farko suka take masa baya.....       A hankali ƙofar corridor ɗin ta buɗe. Sai kowa ya sake nutsuwa da zubama ƙofar ido musamman Imran, Faro, shugaban prison. Yaran sojojin uku da suka rage a wajen kawunansu a ƙasa na girmamawa. Sakan goma tsakani jarumin jarumai ya bayyana, bayyanar data saka gaba ɗaya sojojin wajen harda su Imran ƙamewa a tare suka sara masa.Sai da ya lumshe idanunsa ya buɗe a kansu, sannan shima ya dunƙule hannaye duka yana ɗan miƙasu gaba alamar amsar girmamawar su. A karo na biyu, shugaban prison, Imran, Faro suka sake ƙamewa da sarawa irin ta girma da girma. A yanzu kam shima sai ya ƙame ya sara musu su ukun murmushin mai nauyi ya bayyana a fuskarsa. Kai tsaye ya saka idanunsa cikin na Faro da shima ke murmushi, ido ɗaya Faro ya kashe masa da sake yin wani salute na abokantaka da amintaka.       Dada ya girgiza kansa yana murmusawa da yima Faro alamar (bazaka taɓa canjawa ba) da idanunsa. Sai kuma ya janyesu a slowly ya maida kan Imran da ya tsaya cak kawai yana kallon sa shima. Idanusu ne suka haɗu cikin juna, shekaru takwas na ɓacin rai, rashin adalci, fushi da raɗaɗi duk suka bayyana cikin wannan idanuwa huɗun tamka a film ɗin da aka dannama pause.       Zak-Shadow ya sakarma Imran murmushi cikin nauyin zuciyar da ya saba ɓoyewa.      “…Imran Abbas?”.    Dada ya faɗa a karo na farko da wani irin salo na jini yaga jini.       Imran ya saki murmurshi tare da matsawa kusa da shi gab, sai kawai ya rungumeshi.          “Shagwaɓaɓɓena”.      Dada ya faɗa cikin kunnen Imran jin saukar hawayensa akan kafaɗarsa. Share hawayen yayi sannan ya ɗago yana murmurshi.        “Alƙawarin ALLAH ya cika. Rubutacciyar ƙaddara daga littafi na gaskiya ta taƙaita. UBANGIJI ya tabbatar mana zai jarabcemu, sai dai da jarabawar nan zai ɗaga darajojinmu a sama idan mun kasance masu haƙurin cinyeta. Ƙasarka ta jira dawowarka. Zuri'a bata manta da kai ba. Rundunar soji na kwatance da sunanka. Bararka da zuwa mai son a gina gaskiya a zartar da ita koda zata ƙona kai da kai. ALLAH ya cigaba da amintar da wannan RUHIN bisa kyakkyawan gini na gaskiya. A yau zan buɗe muryar data disashe saboda kukan kewa na faɗama duniya cewar Haysam Abdul-rasheed Shehu is back again”.         Murmurshi Dada ya saki mai nauyi, zuciyarsa ta rikice da son fitar da abinda ke zagaye da ita na kewa tsahon shekaru, ba dan prison ba, ba don wahala ba, sai dan kalaman Imran dasuka ratsata har cikin jini da jijiya dama ƙashi. Amma da yake mazan maza ne sai suka rikiɗe da ƙarfafa kai bayyananne. Da nayin kamewa da nutsuwa ya furta,        “Imran! You are my destiny. I am proud of you........✍️ Received at 12:27 PM [01-16, 11:37] +234 703 449 6321: 34 ..........“Almu na maka kiran gaggawa ne saboda ƙarin abokin aiki da zaka samu”.     Cikin tashin hankali maigadi ya ɗago yana kallon mutumin dake zaune cikin lallausar kujerar ƙayataccen falon. Sai kuma ya sake maida kan nasa ƙasa da sauri. Zuciyarsa na bugawa da yin rawa a cikin ƙirjinsa ya furta, “Ranka ya daɗe nawa aikin baya tafiya dai-dai ne?”.         Sai da mutumin yaja fin sakan uku kafin ya amsa cike da isa. “Aikin ka na tafiya dai-dai Almu, anzo gaɓar da shima wannan ɗin dole sai ya shiga gidan ne”.      “Shike nan ranka ya daɗe, yanda kace haka za'ai. Ni dai ALLAH ina sake roƙon arziƙi kada a cutar min da ƴar uwa. Kaima ka sani mu marayu ne, bamu da kowa a wannan duniyar sai kammu mu biyun nan rak.”           “Bijirema umarni na ne kawai zai iya sakawa ta cutu. Idan ka kiyaye ta kiyaye lokaci kaɗan ya rage muku ku samu freedom.”       “Zamuyi duk abinda kake buƙata in sha ALLAHU ranka ya daɗe. Amma dan ALLAH zan iya ganinta?”.      Wani banzan kallo daya saka maigadi sake nutsuwa mutumin ya watsa masa. Sai kuma yaja tsaki yana ɗaukar wayarsa dake gefe yay danne-danne. Kunnensa ya kai, sai dai a taƙaice ya furta, “Zaka iya fitowa”. Daga haka ya ajiye wayar. Shiru falon ya ɗauka, sai ƙarar tv dake fita ƙasa-ƙasa dana ac. Cikin abinda bai gaza mintuna biyar ba wani ya fito. A ƙalla dai bazai wuce shekara talatin da shida ba. Shima cike da tashi izzar yay ma Almu kallo ɗaya ya ɗauke kansa. Sai da ya zauna a kujera sannan wancan mutumin dake kallonsa fuska da murmurshin da tun da Almu ya shigo bai gani a fuskarsa ba.       Almu ya nuna yana gyara zama. “Wannan shine mutumin da nake gaya makan. Yana aikin gadi a gidan kusan shekara huɗu ke nan, bayan mun tsige wancan ganin bazai iya mana komai ba.”       “Shi wannan yana yin abinda ake so kenan?”. Saurayin yay magana a karo na farko.     “Tabbas yana yi, dan tunda ya fara aiki babu wani kuskure da zance mara daɗi. Sunansa Almu.”       “Okay”.   Ya faɗa a taƙaice. Mutumin bai nuna ya damu ba ya cigaba da faɗin, “Zaka shirya ne ku wuce tare? Ko zaka bishi daga baya?”.       “Kawai mu wuce taren, ai da zafi-zafi ake dukan ƙarfe. Sai dai ya kamata nasan wane aiki zan iya samu a gidan?”.       Yanzu kam mutumin baice komai ba, illa juyawa da yay shima ya kalla Almu. Da sauri Almu yace, “Ranka ya daɗe sai dai in munje can ɗin, amma a yanzu gaskiya a gidan nan babu wani aiki. Dama a wata biyu daya wuce ne driver ɗinsu ya samu hatsari to da an samu sai ya maye gurbinsa. Amma yanzu ma inada tunani guda, akwai mai sharar tsakar gidan kullum da bama filawoyi ruwa. Yakan zo da safe yayi ya dawo da yamma. Sunyi-sunyi ya dinga zama nan koma kwana yaƙi, acewarsa yana wasu ayyukan ne idan ya kammala da nan. To ko shi zamu tunɓuke ta hanyar maƙarƙashiya sai shi ya maye shi?”.         “Eh wannan ma kazo da zance mai ƙyau. Amma miyasa ban san da labarin driver ba? Bayan kuma na sanar maka ko sabuwar kaza akai a wannan gidan nasan da ita. Ko cokali ya faɗi nasan da sautin ƙarar faɗuwarsa....”      “Ka gafarceni ranka ya daɗe, na nemeka amma ban samu ba, idan baka manta ba jiya daka turo min saƙon kana son ganina na tura maka amsa da dama inada wata magana. To dama maganar kenan”.       Maimakon amsa zancen sai cayay, “Kaje waje ka jira shi zai fito”.       Idanun Almu cike da ƙwalla ya jinjina kai. Yayi kamar zai miƙe sai kuma ya sake komawa ya duƙa. “Ranka ya daɗe dan ALLAH ko zan iya ganin ƴar uwata ɗin?”.          “No!”.    Ya bashi amsa a ɗan tsawace. Da sauri maigadi ya miƙe jikinsa na rawa ya fice a falon. Idanunsa kuwa tuni sun cika da ruwan hawaye. Zuciyarsa kam raɗaɗi take masa. Tabbas badan da ƴar uwarsa da mutanen nan suke amfani wajen juyashi yanda suke so ba sun san basu isa ba. Shine fa Almu, Almu na babba ƙarfe bashi ratsa jininka. Guduma mai fasa kan tantiri.... Ƙwafa yayi yana mai cije laɓɓansa, daga haka ya samu waje a bakin baranda ya zauna...... °°°°°°°°°°°°°°°°°°°° Received at 12:27       “Aunty Shariffa karki damu, lokaci ne zaku sani, amma shagalin biki sai Dada na nan in sha ALLAHU”.      A take falon yay tsitt, Dan shima yayi maganar ne muryarsa na ɗan rawa. Mammah ce tai gyaran murya, dan tasan yanzu zasu fara mata koke-koke. Cikin canja hirar ta ce, “Mudai yanzu tashi ka ɗakko mana tsarabar mu nan duk ita mukai zaman jira”.         Cikin dariya Bilal ya ce, “Kai Mammah harda ke? To kowa yay haƙuri baza'a buɗe tsarabar nan ba sai yarana sun dawo school gaskiya. Dan sune zasu buɗe ta”.        “Yau muna ganin jalala, har sai su kafi auta sun dawo za'a bamu tsarabar?”.        Yanda Aunty Lailah tai maganar yasa kowa fashewa da dariya........✍️ Received at 12:27[01-16, 11:37] +234 703 449 6321: 35 .......... ★PRISON★        9:30am dai-dai motocin sojojin biyu suka fice daga cikin prison ɗin cikin tsaro mai cikakken sirri, yayin da hukuncin UBANGIJI da ƙarfin ikonsa suka tabbata a daidai wannan lokacin wani razani ya gitta a zukatan wasu mutane daga ɓangaren Ƙungiyar duhu, a ƙasan rayukansu suka dinga jin cewa abu mafi hatsari ya faru. Sai dai daga ina? Daga wane yanki? Akan mi? A dalilin mi? Duk UBANGIJI ya toshe wannan amsoshin daga garesu, koda ata hanyar yaransu dake cikin prison ɗin babu wani labari da suka samu saboda gargaɗin shugaban ƙasa...... ★A ɓangaren su CSP Alpha shugaban prison bayan fitar motocin su Imran biyu sai wajen ya sake nutsuwa takar an ɗora dutse a zukatansu, ga iskar da suke shaƙa ji suke kamar ta rikice da wani irin nauyin da babu mai iya fassara shi. CSP Alpha bai iya ya motsa daga tsayen da yake ba har bayan an kulle ƙofar gate ɗin. Jikinsa ya ƙara sanyi, numfashinsa na fita a cure, zuciyarsa ta kumbura cikin ƙirjinsa. Jin tamkar hajijiya na neman zubar da shi babu shiri ya jingina da bango kaɗan, hannunsa na riƙe da takardar Presidential Pardon da yake jinta da uban nauyin da yafi na takarda a hannunsa, ta koma mata tamkar nauyin dutse ne.        Dai-dai nan wani sojan da ke tare da shi ya matsa kaɗan yana son yin magana, amma CSP Alpha ya kaɗa masa ido cikin gargaɗin tsoro da rashin tabbas....        “Ka tafi! Ku tafi ku duka…!” Muryarsa ta fita da ɗan kauri cike da bada umarni irin na manya. Kai tsaye sojojin suka bar wajen, sai dai zukatansu nata tsalle-tsalle, tsallen da suka tabbatar da in ya wuce zuciya yace zai zo kan harshe zasuyi nadama ne ta har abadan. Dan haka kowa ya ajiye abinda yaji ya kuma gani anan dan wata shirun tafi alkairi. Musamman ma daya kasance an musu gargaɗi na haƙiƙa dan tamkar an zaɓesu ne akan al'amarin...       Sai a lokacin shima CSP Alpha ya tuna da maganar da shugaban ƙasa janar Yusuf ya yi masa kwanaki biyu da suka gabata a cikin waya…       “Ka kiyaye sirri fiye da kiyaye rayuwarka. Idan ka yi kuskure, ba zan iya kare ka daga hukumar tsaro ko daga mutanen dake a waje suna jiran Zak-Shadow ba. Kuma wlhy duk wanda ya san wannan al’amari kafin lokacin da ya dace, to kai kanka ka yi masa jagora zuwa lahirarsa”.       Wannan kalamai ne da har cikin jinin CSP Alpha suke da tasiri mai saka razani da ƙaulanin zuciya har yanzu. Ya sauke ajiyar zuciya mai nauyi, goshinsa ya cika da zufa. Hannu ya kai ya sharce gumin, kafin ya furta da ƙasa-ƙasa kamar mai roƙon iska. “Ya ALLAH an sakani a tsakiya?. Wane irin mutum ne wannan Zak-Shadow ɗin da shugaban ƙasa ya zo kan al'amarinsa haka da gaggawa?”.       Bashi da amsa, babu kuma mai bashi ita a yanzu. Dan haka bai yiwa kansa dogon tambaya ba ya haƙura. Tsoron da yake ji game da maƙudan mutanen da ke bayan fage ya fi ƙarfin neman amsoshin tambayoyin nan dake danƙare a zuciyarsa....... <<<%>>><★><<<%>>>        Tunda suka baro cikin prison ɗin shiru ya ratsa motar, sai sautin AC da numfashin su dake fita iyakar motsin ƙirazansu. Baradan jaruman haziƙan sojojin uku Imran, Faro, Zak-Shadow. Ba wanda ya ce komai. Kowa da abin da yake tattaunawa da zuciyarsa.       Sai rufaffen gilashin motar da ke nuna hasken rana daya fara zafi, launin duhun sa ya bayyana fuskokinsu dake da sanyin annuri.       Daddy Imran yana kallon Dada akai-akai tamkar idan ya ɗauke idanun nasa zai ɓace masa ne, ko yana son tabbatarwa wannan ba mafarki ba ne. Faro dai sai murmushi yake yi irin wanda yake nuni da cewa (Na gaya maku wataran ƙaddara da ƙarfin ikon wanda ya fiku iko zai dawo da shi a duniyar ku).       Amma shi Dada ya rufe idanunsa cikin nutsuwa, yana fitar da numfashi a hankali da shaƙar mai tsabta fiye da duk wanda ya shaƙa a cikin shekaru takwas. Yawan jin idanu a kansa dan in har ana kallonsa sai yaji a jikinsa, balle wannan kallon yana jin ƙarfin idanun mai su a cikin ƙirjinsa. Ya kuma tabbatar da Imran ne ke da wannan tasirin. A hankali ya buɗe idanuwan nasa, sai ko suka sauka kai tsaye akan Imran ɗin da yay hasashe. Hararasa ya ɗanyi, tare da ɗage masa gira ɗaya, da murya ƙasa-ƙasa amma cikin zurfi ya furta, Received at 12:27“Kallon fa?”. Ƙaramar dariya Imran yayi da faɗin, “Ina tsoron karka sake ɓace min ne”. Kauda fuska Dada yay kaɗan da sakin ƙaramin murmushi, batare daya tanka batun Imran ɗin ba ya sake jeho masa sabuwar tambaya. “Motar nan ina take son kai mu?” Daddy Imran ya ɗan taɓe baki da matsawa kaɗan ya jingina da kujera. Shima cikin salon raɗa ya ce, “Wurin da ba wanda zai same ka. Wurin da babu ƙungiya, babu siyasa, babu duhu. Wurin da zaka samu iska ta ƴanci bayan shekara takwas daka rasa”.        Dada ya girgiza kai a hankali tare da lumshe idanu ya buɗe a lokaci guda. “Na gode muku Imran, Faro, na gode sosai.”      Kafin Imran yace wani abu Faro ya katse su cikin siririyar dariya mai armashi da jin daɗi. “Zaki wlhy idan ka sake irin wannan sakon godiyar, zan fara tunanin da gaske zaka canja halinka.”     Dada ya kalle shi yana murmushin ƙasaita sai kuma ya maida kansa ya kwantar a jikin kujera ya lumshe idanunsa har lokacin da murmushi a kan fuskarsa. Sai a lokacin ya furta, “Ga shi kai baka da ranar canzawar da wannan sa idon naka”.        Dariya Imran da Faro suka sanya, cikin irin dariyar da ta bayyana ƙyallin ruwan hawaye daga idanun Imran da ya kasa ɓoyewa....        Dada dake murmushi zuciyarsa ta tafi sabon tunani. (Shugaban ƙasa da kansa ya yanke wannan hukuncin da gaggawa? Mi yasa? Mi ya faru da ƙasata cikin wannan lokacin? Mi ake shirin bani? Mi ake buƙata daga gare ni?). Kafin ya samo amsoshin waɗan nan tambayoyi masu nauyi Imran ya katse shi da faɗin, “Muna da tsaro mai ƙarfi, babu wanda zai kusance ka har sai ka shirya. Koda likitoci sun gama duba ka zaka cigaba da zama a ɓoye. Babu wani abu da zai kusanto ka. Sai mun kammala gyara rashin adalcin da aka yi mana, dan ƙasa tana buƙatar komawar ka a Zak-Shadow ɗin data sani ne. Mammah zatafi farin ciki idan ta ganka a Haysam ɗinta itama. Balle kuma ƴaƴan Dada”.      Dada ya ɗan furzar da numfashi da buɗe idanunsa dake a rufe, zuciyarsa cike da wani nauyin da bai gama wargajewa ba. Tabbas a yanzu ba wanda ya fi buƙatar son fara gani kamar Mammah da ƙannensa, amma zai daure ya jure dan yasan duk yawan kwanakin da suke so yayi anan bazasu kai yawan wanda yayi a baya ba. Shima zai fi son Mammah ta gansa cikin ƙyaƙyƙyawan kamanni ba wannan kamannin da yake a yanzu ba da zasu iya raunana zuciyarta har ta gagara mantawa da su. Numfashi ya sauke a hankali, a yanayinsa na Zak-Shadow da suka sani ya furta, “Imran kun tabbatar babu wanda ya san dawowa ta?”.      “Ai ko motar nan ta bari wasu suka ji Zak-Shadow ya dawo, ta riga ta mutu.” Imran ya ƙare maganar yana dariya mai taushi. Faro ma hannu ya ɗaga yana dariya da faɗin, “Duniya zata san dawowar ka ne lokacin da ka yanke hukunci, ba lokacin da kowa yake jin yanada ƴancin faɗar abinda ya gani ba koda Imran da Faro da shugaban ƙasa ne.”          “ALLAH ya shiryeku, yau kuma kun zama ƴan comedy”. Cewar Dada yana ɗaukar takardar dake gefensa. Yanzun ma dariya suka sanya, dan har ƙarƙashin zukatansu suke jin wannan nishaɗin mara misali. Shi kansa Dada yana jin fiye da nasu, kawai dai ya fisu kamewa ne, sannan halayyar su dama can ba ɗaya bace, su sunada faran-faran da magana, sabanin shi da ko wasa bai iya ba, dama dai da Imran ne wani lokacin idan ya matsa masa, sai shima Faro ɗin idan ya gallabesa wasu lokutan yakan maida musu murtani.....       ⭐ 10:43am dai-dai Motocin biyu suka isa secret medical base wuri na musamman mai tsafta, nutsuwa, da ƙa’ida. A yanda gurin yake a killace zaka ɗauka Shugaban ƙasa yasa an tsara shi ne tamkar dan ɓoye Dada ɗin ne anan. Dan tuni har likitoci suna jiran su, likitoci kam na musamman ne aka tanada dan duba lafiyarsa, saboda duk ƙarfin halin da Dada ke nunawa su sun san abu na farko da yake buƙata shine duba lafiyar tasa.        Sun masa tarba ta girmamawa suma, dan duk da halin da yake ciki kwarjinin yawan ibada da UBANGIJI ya bashi yana nan a tare da shi sai ma ƙaruwa da yayi da sake ɗaga darajarsa ga duk mai kallonsa. Received at     Shi ɗin DODO ne a kowane irin yanayi, dan haka a nutse yake bin komai da aka shirya da nazari irin na masu nutsuwa: Kayan aiki, ma’aikata, da tsaro mai ƙarfi. Sai da Idanunsa suka gama tantance kowanne daga cikinsu, kamar yadda yake nazarin duk wanda zai shiga cikin binciken sa.       Imran dake lure da shi ya saki murmurshi ya juya kansa zuwa ga Faro. “Faro, ka tabbata babu wanda zai san dawowar sa.”      Faro daya fahimci saƙon da Imran ke son isarwa ya ɗaga hannu tare da kashe masa ido ɗaya ya ce, “Babu wanda zai sani, har sai lokacin da Zak-Shadow ya yanke hukunci.”        “Kayi ƙyan kai Faro. Lokaci zai bayyana komai da kansa. Duk wanda ya ga fitowarsa ba a shirye ba kuwa zai zama....” Imran yay alamar mutuwa.       Su suke maganar, amma Dada nazartar likiticin daya tabbatar su su Imran kema wannan zaurancen yake. Ganin yanda suka duƙar da kawuna yasa shi fahimtar suna fahimtar komai suma. Baiyi magana ba yay gaba kai kace yasan wajen ne. Da sauri likiticin suka zabura dan masa jagora, Imran da Faro suka sake kallon juna da murmurshi, sai suma sukabi bayansu..........✍️ Received at 12:27 PM [01-16, 11:37] +234 703 449 6321: 36 ........Ciwon kai sosai ya gallabi Nimrah a makaranta saboda raunin kanta da bai gama warkewa ba. Babu shiri wajen sha biyu aka maidata gida bayan an kaita clinic ɗin cikin makaranta sun dubata. Ba ƙaramin tashi hankalin su Mammah da su Aunty Ummi dake gidan yayi ba. Dan duk ciwon da zakaga ya kwantar da Nimrah haka ba ƙaramin jinsa take ba. Ga jikinta zafi zau da zazzaɓi. Mammah ɗakinta ta Kaita ta kwantar bayan kowa ya gama jera mata sannu da addu'a. Da kanta ta zame mata uniform ɗin jikinta ta barta da vest da shot kawai, ita ta goge mata jiki da ruwan sanyi tasa aunty Mimi ta ɗakko mata riga mara nauyi a ɗakinsu. Aunty Shariffa ta kawo mata kunun madara, da ƙyar aka lallaɓata tasha tana hawaye dan ji take kamar kan zai rabe mata biyu, kaɗan tasha kunun tasha magani Mammah ta kwantar da ita tana tofa mata addu'a har barci ya ɗauketa...... <<<<<★★★★>>>>>              “Sir na bincika kamar yanda kace. Gidan nan gidan wani soja ne, akwai mahaifiyarsa a ciki da ƙanensa, amma shi yana ɗaure shekaru takwas kenan. Ita kuma yarinyar ban sani ba ko ƙanwarsa ce ko ƴa gaskiya. Dan ban samu wani cikakken bayani a kanta ba, a dai gidan take, kuma ƴar gidan ce”.      Gaba ɗaya ma'aikacin hotel ɗin yayima Adeel bayanin ne da harshen turanci, dan da shi suke magana kasancewar shi baya jin yarensa shima baya ji, amma dukansu sunyi tarayya akan yaren turanci. Ajiyar zuciya Adeel dake saurarensa ya shiga saukewa. Dan tun marecan jiya da yaga Nimrah bai sake jin cikkiyar nutsuwa ba a zuciyarsa. Yau ɗin nan yana da zama da tsohon shugaban ƙasa, amma bai iya yaje ba saboda ba waccan damuwar bace yanzu gabansa ta yarinyar da ko sunanta bai sani ba ce. Hatta su Nabeeha bai sake bi takansu ba. Ko wanda yasa yana bibiyarsu da yazo da safen nan masa bayani kamar yanda ya bashi umarni cayay yaje kawai yana buƙatar hutu.      Da turancin ya ce, “Miye sunanta?”.         “Nimrah!”.     Sai da ya wani lumshe manyan fararen idanunsa ya buɗe sannan ya saki murmurshi. Dan kuwa sunan ya dace da ita. Dan a cikin sakannin da suka haɗu ya tabbatar da ita ɗin zakayyarce, zuciyarsa ta shiga wassafo masa ɗan mitsitsin bakinta na tsiwa mai ɗauke da kyawawan lips pink da baƙi. Yanda ta zazzaro masa dara-daran idanunta farare tas masu suffar ƙwai da masa gargaɗin kada ya taɓata da yaren da bai gane komai ba. Ya saki ƴar dariya da sake hango idanunta da suka watsa masa harara.      Galala ma'aikacin hotel ɗin yay hana kallonsa, dan lallai ya yarda wannan guy ɗin ya faɗa da yawa. Koda yake baiga laifinsa ba. Dan yaran fa sun haɗu, su duka biyun wanke hannu ka taɓa ne. Daga gani kasan ƴan hutu ne kuma ƴan gata ƴaƴan manyan ƙasa. Duk da basu wani gama cika manyan ƴammata ba ko a haka za'aje da su, damma a cikin hijjab suke ba komai nasu ake gani ba face fuskoki.....       “Ka samo number wayan ta?”.   Adeel ya katse masa tunani. Kansa ya girgiza da faɗin, “A'a Sir, bayan waɗan nan bayanan babu abinda na samu gaskiya. Dan gidan nan ba ƙaramin gida bane da samun information ɗinsu zai mun sauƙi. Wannan ma sa'a akaci na ga wanda na sani a street ɗin, shima kuma bai wani jima da kama haya ba.”       “Good kaje ka zomin da shi”.   Kai ya jinjina masa a ransa yana mamakin irin wannan haukacewa haka daga ganin yarinya? To amma ina ruwansa, aikin kuɗi yake yi, ya tabbatar kuma idan Adeel ya samu abinda yake so shima zai ja kaya. Dan Vvip ɗin da ya kama kawai ya isa ya sanar dakai mugu-mugun mai kuɗi ne shi. Balle manyan agogo da designers kayansa zuwa takalmi, kai wayar hannunsa kanta kai kasan lallai akwai manda. Dan zai iya rantsuwar bai taɓa ganin irinta ba balle kamfanin da ake yinta. (😜Ƙaryar marubutan ta motsa anan. Ya kuka iya🤣 ku karanta kawai🥱. Amma in gaskiya za'abi ai akwai masu kuɗin nan dai ko🥱😎).     Hannu Adeel ya ɗaga masa, ya ɗan risina na girmamawa sannan ya fice.....    >>>>>>>%<<<<<<<        Kamal na ƴar dariya da shafa kai ya ce, “To kusan haka baba, amma ai da sauran lokaci tunda nasan baza'a mata aure yanzu ba nima kuma haka”.      “Kai! A wannan shekarun naka?”. “Baba tsahon ƙafa ne kawai, amma ba wasu shekaru bane dan ashirin da biyar ne kacal”.         “To ai sune dai-dai auren ɗana. Mutum ya more yanda yake so ba auren bariki ba sai an gama tsofewa a ɗakin soro. Mu kaga iyayenmu sun mana gata a sha tara ma suka mana auren”.      “Baba sha tara fa?”.   “Sosai. Ba gashi mun mora auren yanda ya kamata ba. Itama kuma ai in a ƙauye ne yanzu ta isa haihuwa ma ta biyu ko ya yaye na farko tana da cikin na biyu. Shekara sha biyar fa tana cikin ta sha shida koba haka ba?”..           “Tabbas haka ne Baba”.     “To ka gani, ai karka wani damu kanka, ka fara yaɗa manufa kawai muma zamu tayaka”.     “To baba ALLAH ya tabbatar mana da alkairi”.      “Yawwa haka nake so naji ka faɗa”. Cewar Malam Buba yana miƙewa. Ya cigaba da faɗin, “Kaga jirani bara na kirata, dan naga kwana biyu ma bata zuwa makaranta sunce bata da lafiya. Kwana kusan biyar kenan taji ciwo a islamiyyar su ne...”      Cike da jimami Kalam ya amsa masa da, “Haka ne Baba, wlhy a islamiyya ne fa.....”    Ya kwashe labari tsaff ya sanar masa. Malam Buba dake saurarensa cike da nazari yay wani murmushi mai ma'anoni da yawa. Dan kuwa tabbas yau ya samu hanya mai sauƙi da yake nema da fata. Tabbas Kamal shine zai kasance makamin amfaninsa akan cimma burinsa kan Nimrah. Labarin nan kuwa yay masa matuƙar daɗi da ɗaukar hankalinsa. Tuni ya nufi cikin gida kiran Nimrah.........✍️ Received at 3:59 PM[01-16, 11:37] +234 703 449 6321: 37 .........Imran ya miƙe kenan zai wuce Malam Buba yay sallama. Amsa masa suka yi shi da Mammah, kafin Mammah ta bashi izinin shigowa. Koda wasa bai kalla sashen da Imran yake ba, dan haka kawai yake jin tsarguwa idan Imran ɗin na kallonsa. Daga bakin ƙofar ya rissina ya gaishesu, sannan ya isar da saƙon Nimrah tayi baƙo.       Cike da mamaki a tare Mammah da Imran suka furta, “Baƙo kuma?”. Har yanda sukai ɗin ya bama Malam Buba mamaki. Amma sai ya shanye mamakin nasa yay ƙarin bayani da, “Yace malamin su ne na islamiyya, mage ce ya kawo mata, yace kuma itace da kanta ta buƙaci haka.”      Mammah tasan labarin mage, dan har Nimrah a kwanakin tana mitar batun kawota da malaminsu baiyi ba. Kusan yanzu ma take jiyosu daga kitchen Nimrah na batun da tasan number sayyadinsu data kira a wayar Biebah ta tuna masa batun magenta. Sunan Nimrah ɗin ta kira, ta amsa tana fitowa daga kitchen ɗin hannunta da kofin tea, ganin sabon driver ɗin su da ko sunansa bata riƙe ba har yanzu ya sata ɗan tsayawa turus, sai kuma ta ɗauke kanta daga kallonsa ta ƙaraso wajen Mammah.       Hannu Mammah tasa ta amshi kofin shayin hannun nata tana faɗin, “Saka hijjab kije ga malamin ku yazo kawo miki magen taki”.       Washewa fuskar Nimrah tayi da murmushi, cike da farin ciki ta ce, “To Mammah. Ta ɗauki hijjab a inda suke ajiyewa ta saka. Malam Buba na gaba tana biye, haka kawai ta samu kanta da zubawa bayansa ido duk da zuciyarta dake bugawa. Imran na daga ciki sallama yay ma Mammah ya fito dan kiran Faro nata shigo masa a waya, yasan kuma zai iya yiwuwa Dada ne, shi kuma baya son ɗagawa a gaban Mammah dan ko a fuska bai nuna mata fitowar Dadan ba. Dai-dai Nimrah na kaiwa gate, cikin ɗan risinawa ta gaida Sayyadi Kamal daya zuba mata ido. Ita kam kanta a ƙasa batama san yana yi ba.         Idanu sosai Imran ya zubama Kamal ɗin daga inda yake tsaye cike da nazari, yayinda shi kuma hankalin Malam Buba yake kan Imran a kaikaice shima yana nazarin kallon da yake ma Kamal ɗin. Nimrah kam bata ɓata lokaci ba ta miƙa hannu amsar kwalin magen. Kamal na murmushi da kallonta ya miƙa mata tare da miƙewa, kaɗan ya matsota yana magana ƙasa-ƙasa. Nimrah ta yamutsa fuska da ɗan jan jikinta baya, yayinda fara'ar fuskarta ke raguwa alamar maganar daya gaya mata ce batai mata ba. Dan kamar wadda take a ƙage ma yana sakar mata kwalin ta baro wajen tana masa sallama da tafiya duk a lokaci guda. A haka ta ƙaraso inda Imran yake tsaye yana kallon Kamal dai dake binta da kallo..        “Daddy kaga mage na”.    Nimrah ta faɗa dai-dai tana isowa gabansa, murmushi ya saki yana ciro hannunsa daga aljihu ya amshi kwalin cike da kulawa. Da kansa ya kwance ɗaurin zaren da akaima kwalin yasa hannu ya ciro kyakkyawar magen fara tas ƴar ƙarama.        “Masha ALLAH Babyn daughter ta iso gida lafiya. ALLAH ya rayata ta haifa mana yara da yawa duk a raba mana”.      “Amin Daddy”. Nimrah ta faɗa cike da farin ciki. Maida mata ita yay a kwalin. “To ya sunanta?”.       “Uhmm Daddy sai Ruky ta dawo zamu saka mata suna”.      “Oh na manta, Ussaina bata yanke hukunci sai Hassanarta na nan. Bari na wuce idan an saka sunan maji a waya”.           Nimrah na dariya ta ce, “Daddy ALLAH ya tsare hanya. Ka gaida Ammie da su Aunty Ma'u gobe zamuzo daga nan muje gaida Grandpa tunda Grandma taƙi dawowa daga ƙauye. Sai mu wuce mu gaida Ummu da Grandpa suma ko”.       “Tunani mai ƙyau Daughter, ALLAH ya kaimu. Amma ki kwantar da hankalinki ma su Asma'u suna hanyar zuwa nan gaida Mammah suma.”      Wani irin farin ciki ya sake kamata. Tai ciki tana murna da faɗin zataje tai ƙwaɓa fulawa nayin ɗanwake da kalallaɓa”.      Fuskarsa da murmurshi ya bita da kallo harta shige. Kasa riƙe abinda yake ayyanawa a zuciyarsa yayi sai da ya ambata, “My Zaki ɗiyata ta zama macen nan da kake tunanin za'a jima bata kai ba, Abu na farko kenan da zai fara baka mamaki idan ka taka ƙafarka a gidan nan”. Sai kuma ya sake sakin murmushi yana girgiza kai saboda hasaso cakwakiyar dake gaba. Har yanzu Nimrah bata san akwai aure a kanta ba, shiyyasa suke kaffa-kaffa da al'amarinta ko nan da can ba'a barinsu zuwa su kaɗai sai da driver ko Mu'azz.. dai-dai yana isowa wajen motarsa, kallon da yaron nan da akace malaminsu ne ya faɗo masa a rai. Juyawa yay ya kalli gate ɗin, sai yaga sabon drivern nan daya sakama alamar tambaya ne kawai a wajen yaron baya nan alamar ya wuce. Lallai dolene yay saurin tsaida wannan alaƙar, dan ya lura akwai wani abu mai girma a idanun yaron game da Nimrah. Mota ya buɗe ya shiga, bayan an buɗe masa gate ya fice yana mai kallon agogon motar dan yana son daga massalaci ya ziyarci Janar ne su tattauna batun ƙarasowar Zak-Shadow gida tunda likitoci sunce bawani damuwa, sai dai sakamakon gwaji ɗaya da ake jira kawai yau ya fito suji...... >>>>>>%<<<<<<               Bayan sakkowa massalacin juma'a gidan Mammah ya kacame da hayaniya. Tuni su Ruky sun dawo gida, ga yaran gidan Uncle Nasiru da matarsa Hajiya Zuwairah da kowa ke kira (Ummu). Yaya Imam, Aunty Halimatu, sai ƙawa aminiyar su Ruky Bintu, da autoci Sadiq da Adam. Hakama daga gidan Daddy Imran akwai Babban Yaya Haysam da suke kira Khalifa, sai Asma'u dake bimasa suna kiranta Aunty Ma'u, Ruƙayya ke bima Asma'u, sai Auta Marwan suna kiransa (Lolo). Yaran Aunty Ummi huɗu suma sun iso, Firdausi itace ke bima Mu'azz, itama sa'anni suke da su Nimrah, sauran uku duk maza ne. Abdul-rasheed suna kiransa Dady, sai Harun, da auta Saddam. Sai na Aunty Mimi itama uku. Ita kam duk maza ne da ita jinjirarta ce kawai nace a yanzu, Fu'ad, Salman, Ishaq. Sai na Aunty Momy huɗu itama. Maza biyu mata biyu. Kasancewar mazan sune manya matan sai suka kasance ƙanen su Nimrah. Itama tana da Na'eem, dan sunan surukinta yaci suke kiransa Na'eem, sai Sauban. Matan Nusaiba, da Khairat.        Tunda aka kammala kaya-kayar cin abinci kowa yaja sa'anninsa suka dasa hirarsu. Halimatu da Asma'u suna tare da Aunty Biebah duk da dai ta girmesu, sai dai da yake suma sun gama cika ƴammata sunfi su o'e ƙwailoli iyayen kankanba da rashin ji nustuwa😂. Sai Imam, Mu'azz, Khalifa suma suna ɗakin Mu'azz abinsu matasan samari kenan ƴan shiga jami'ar bana. Suma sauran na ƙasan kowa yaja tashi da irar sai ƙananun sosai su Afrah dake manne da Mammah da Ummu.       Ƙawayen juna masu ji da tashen farkon balaga ma dai suna can sun kulle kansu a ɗaki ana cafta. Nimrah, Ruky, Bintu, Feedo. Kai da kaji yanda suke hirar kasan basa ɗaukar kansu fa ƙwailoli sai manyan ƴammata. Dan Feedo ke basu labarin saurayi da tai cousin ɗinsu daya dawo daga karatu Saudiyya shine fa aka baje kolinsu cike da iyayi ana cafkewa......          ++++++++++++++        Da ƙyar abokin ma'aikacin hotel ɗin nan ya yarda ya biyoshi kiran Adeel, sai da yazo yaga kuma mai kiran nashi duk ya rikice. Dan duk da bai san waye Adeel ɗin ba a zahiri abubuwan dake zagaye da shi ya tabbatar masa wani shegen duniya ne.        Cike da gadara kuwa Adeel ya ajiye masa rafofin kuɗi masu kauri yana sanar masa buƙatarsa akan gidan da yake zaune yake son ya bashi wajen zama a ciki. Sannan ya masa bayani akan gidan su Nimrah. Gaye yaga kuɗi duk ya gigice, yo dala wasa ce. Jiki na rawa ya tabbatar masa da ya amince yazo su zauna. Batun gidan su Nimrah kuwa yace shi ba komai ya sani game da su ba gaskiya, amma yana gaisawa jefi-jefi da wani yaron gidan da safe idan ya fito zaije jugging shima zai je.          Fuska a ɗan yamutse Adeel ya ce, “Ba damuwa wannan alaƙar ɗin ta wadatar. Zamu iya wucewa gidan naka yanzu, dan bana son ɓata lokaci. Miye sunan ka?”.      Da ɗan rawar baki yana kallon abokinsa ma'aikacin hotel ɗin ya ce, “Yohana!”.           “Okay yayi, zamu iya tafiya”.      Duk da zuciyarsa na rawa haka ya amince, dan shi da abokin nasa ma suka ɗauki ƙaramin traveling bag ɗin Adeel ɗin daya kasance ƙaramin troly ne zuwa harabar hotel ɗin. Sai dai yabar wasu ɗan abubuwan sa a ɗakin hotel ɗin dan haka da card ɗin buɗe ƙofar ma ya wuce. Kusan ƙarfe takwas suka iso anguwar, ko'ina da haske fes ga anguwar shiru babu hayaniya sai securitys kawai dake kai kawo. Ta gaban gidan su Nimrah suka wuce. Sai Adeel yaji kamar ya sauka anan ya shiga ya ganta. Sai dai babu dama. Tsakanin gidan Yohan da gidan su Nimrah bai wuce gidan huɗu ba. Kuma su suna ɗayan hannun ne ta yanda daga gidajen su Yohan ɗin ma kana iya ganin gate ɗin su Nimrah tsaf musamman idan kana upstairs ne. Can ma gate aka buɗe musu suka shiga, da yake wani ɗan ƙaramin estate ne yake, mai ɗauke da apartment da basu wuce goma ba gaba ɗaya.........✍️ Received at 3:59 PM Viewed 1 time [01-16, 11:37] +234 703 449 6321: 38 ..........“Tofa, gyaran gidan nan aka sake yi haka Aunty Nabeeha?”.         Ɗago kai Nabeeha da hankalinta ke kan wayarta tai ta kalla gidan a karo na farko. Ba ƙaramin ƙyau gidan yayi ba kam dan tun daga waje zaka shaida hakan, flowers ɗin da suka ƙawata katangar gidan ta wajen kawai abin kallo ne, ƙamshinsu ya cika wajen sosai kuma. Balle baƙin gate ɗin. Ajiyar zuciya Nabeeha ta saki a hankali batare da tace komai ba. Ismat da Raihana kuwa suka cigaba da santin su har Malam Buba ya leƙo sakamakon horn da Ismat ɗin tayi dan itace ke jan motar.      Malam Buba bai sansu ba, dan haka ya fito sosai yana tambayar “Su waye ku?”.      Sai da duk sukai masa kallon sama da ƙasa, a yamutse Amima uwar rashin kunya ta ce, “Matar gidan ce da ƙanen ta”.         “Kiyi haƙuri Hajiya kumin bayani yanda zan gane, ni baƙone anan, dan dole zan fara sanar da masu gidan kafin na barku ku shiga”.      Sai a lokacin Nabeeha da taja tsaki ta kallesa a wulaƙance. “Kai sha-sha-sha ka buɗe mana gate mu wuce. Shi gidan ya zama na shugaban ƙasa ne yanzu da ba'a shigarsa sai da doka komi?”.         “Ba haka bane Hajiya, ina kan aiki na ne”.     A fusace Amima ta buɗe ƙofa ya fito, hakan kuma yay dai-dai da isowar taxi wajen. Ba kowa bane a ciki sai ainahin maigadi da baƙonsa. Malam Buba ya maida hankalinsa kansa yana ɗan murmurshi da faɗin, “Alhamdulillahi Malam Almu sannu da zuwa?”.       “Yauwa Malam Buba, mun sameku lafiya? Ya na ganka a waje haka kai da su way....”       Ya haɗiye sauran maganar saboda ganin Amima. “A'a Hajiya ashe kune, sannunku da zuwa. Malam Buba buɗe musu ƙofa ai ƴan gida ne”.       Amsa masa Malam Buba yay yana juyawa, Amima kuwa taja tsaki tana komawa cikin motar dan ta fito ne da shirin wanke fuskar mutumin nan da mari. Sai da motar tasu ta shige Malam Almu ya kalli abokin tafiyarsa da ya ce, “Su kuma su wanene su?”.     Cikin ɗan sauke ajiyar numfashi Malam Almu ya amsa masa da, “Matar Baban yayansu ɗin nan da nake gaya maka sunce yana ƙasar waje ce, sauran ƙanenta ne. Ba zama take a gidan ba sai lokaci-lokaci take zuwa tana iskance-iskancenta. Nama fi shekara uku banga ta sake zuwa ba sai yau”.      Kai kawai ya jinjina masa batare da yace komai ba, daga haka suka shige ciki suma. Malam Buba nata jera musu sannu, ya kawo musu ruwa sannan ya zauna suka gaisa yana tambayar mai jiki. Malam Almu ya ce, “Da sauƙi sosai, ɗan uwana dake Niger yazo ya tafi da ita can a nema mata magani, shiyyasa ƙanina ma ya biyo ni nan dan kar a barshi shi kaɗai. Sunansa Sanda”.         “Kai masha ALLAH, ALLAH ya ƙara lafiya. Malam Sanda sannu da zuwa kaji”. Yay maganar yana bama Sanda hannu suyi musabaha. Hannun shima Sanda ya bashi suka gaisa.. Dai-dai nan Rayhana ta ƙaraso wajen cike da tsawa da gadara ta ce, “Kai wani yaje can sashen ya amso mana key ɗin ɓangaren mu”.     Su duka kallonta sukayi, Malam Buba zai yi magana Malam Almu ya katsesa da faɗin, “Hajiya ai ɓangaren nan babu komai a cikinsa tunda aka kammala aikin gidan nan. Ina ga zaifi ƙyautuwa ku shiga wajen hajiyar da kanku dan tana nan. Ko ta fita ne Malam Buba?”. Yanda yay maganar ƙarshe yana kallon Malam Buba da sigar tambaya ya sashi amsa masa da, “A'a tana nan bata fita ko ina ba. Dan yau ma gidan cike yake da baƙi kamar jikokin gidan ne duk suka zo. Sai dai naga matan su Ja'afar sun fita su kam”.       “To kinji Hajiya, ku shiga kawai zai fi”.     Harara Rayhana ta zuba musu su duka, batare da tace komai ba ta juya ta koma inda su Nabeeha ke tsaye a ƙofar sashen nata suna jiranta. Abinda ta sanar musu ya saka Nabeeha jan tsaki. Cike da takaici ta ce, “Nifa ban son iyayi, to ina suka kaima mutane kayansu?”.         “Muje dai wajen Mammah ɗin sai muji kamar zaifi”. Ismat ta faɗa tana binsu da kallo....        ★Gaba ɗaya falon ya cika da hayaniyar su Aheel dake wasan guje-guje, sunma falon kaca-kaca da tarkacensu. Amma hakan bai hana Mammah dake zaune yin hirarsu ita da Ummu (Hajiya Zuwairah matar Uncle Nasiru) hirarsu ba. Sun juyama ƙofa baya, hakan yasa har su Nabeeha suka shigo falon basu sani ba. Babu tabbacin sunyi sallama ko a'a, sai wani kallon yaran suke a yamutse kamar sunga wasu abin ƙyama. Yaran da suma shigowarsu bai hanasu wasan su ba duk da wasu sun gansu wasu basu lura da su ba, Abees dake bin Ishaq da bindiga da aka zuba ruwa ciki yana fesa masa suka iso inda suke. Ishaq ya shige tsakkiyarsu yana ɓoyema Abees suna dariya, shiko Abees ya cigaba da fesa ruwa har a jikinsu. Cikin wani irin takaici Rayhana ta kwaɗe Abees da marin daya saka yaron sakin gigitacciyar ƙarar data saka su Mammah juyowa da sauri. Dai-dai Nabeeha ta finciko Ishaq dake bayanta ta hankaɗashi kan Abees itama. Wannan al'amari na mari da hankaɗewa yayi dai-dai ne da fitowar Nimrah daga lungun ɗakinsu ɗauke da magenta zata haɗo mata madara. Magen ta dire saman stairscase tayo wajen ranta a ɓace.      Miƙewa Mammah da Ummu duk sukai suna kallonsu, haka sauran yaran tuni sunyi tsit kamar anyi ruwa an ɗauke. Sai khairat ce mai ɗan wayo ta ƙaraso inda su Abees suke da sauri. Isowar Khairat dai-dai da ƙarasowar Nimrah da babu ma wanda ya lura da ita a kaf falon sai yanzu. Kafin Mammah data buɗe baki zatai mata magana tayi kawai sukaji saukar mari mai ƙara a fuskar Rayhana, ba kuma kowa yayi mata shi ba sai Nimrah. Kafin ma Rayhana ta dawo cikin hayyacinta ta watsama su Amima da suka wani yunƙuro kanta a fusace manyan idanunta.      Babu tsoro babu shakka duk da sun fita girman jiki da tsayi, dan ma itama ɗin dai doguwar ce, amma kasancewar sun girmeta nesa ba kusa ba sun fita tsayin. Amma tsabar bushewar idanu ko'a jikinta. Sai ma cike da gargaɗi da kaushin murya ta ce, “Oh zaku rama mata ne?”.       Cikin matsanancin baƙin ciki Amima ta ce, “Ai ba rama mata mari kawai ba duka zaki ci”.          “To bari kema na baki rabonki sai ku rama mata ɗin”. A bazata ta sake sauke wani marin a fuskar Amima. Rayhana ta yunƙuro zata cakumeta tasa ƙafa ta taɗeta sai gata a ƙasa wanwar. Ai ko yaran suka saka ihun dariya suna tafi da tsalle da faɗin, “Aunty Ninah! Aunty Ninah!”.      Inda suke yanzu kam Mammah ta iso, dan Nabeeha ma ta yunƙuro kan Nimrah zata cakumota, sai dai Nimrah ta riƙe hannun nata tana mata kallo mai cike da rashin kunya da tsiwa. Yayinda Amima ta cakumi rigar Nimrah ɗin ta baya, Ismat da hankalinta ya tashi dan ita bata fatan ayi wani abu mara ƙyau ita dake fatan samun fada ta shiga janye Amima tana faɗin, “Wai miye haka dan ALLAH.”         “Nimrah! Sake ta”.    Mammah data iso wajen ta faɗa idonta akan Nimrah. Tashin hankali, duk fa wannan abu dake faruwa su Nabeeha basu gane Nimrah ba, haka ma Nimrah bata gane su ba, dan sanin datai musu na ƙuruciya ne, zuwan da sukeyi jefi-jefi kuwa basu taɓa haɗuwa ba tana makaranta, idan ma sun kwana kasancewar randa suka shigo kawai suke zuwa gaida Mammah harsu wuce bata ganinsu. Suma kuma rabonsu da ita tun tana ƙaramar, tsabar yanda suka tsaneta basu taɓa sha'awar idan sun zo gidan su ganta ba musamman Nabeeha. Sai gashi a yau yarinyar da suka sani mitsila ta zama budurwa, ga hasashen ƙyawu da sukama yarinyar a baya ya tabbata. Dan kuwa Nimrah akwai dogon hanci da ɗan bakinta dai-dai ita, ga manyan idanu farare tas da suka ƙawata baƙar doguwar fuskarta mai cike da tsiwa da rashin tsoro. A tsaye yarinya ce doguwa, duk da ƙirjinta ba wani cike yake taf na wuce misali ba komai dai ya bayyana na yammatanci, dan doguwar rigar jikinta ta fitar da komai, tun daga tudunsu har zuwa shafaffen cikinta da kugunta mai faɗi kaɗan dake tabbatar da nan gaba shekaru suka ƙaru zai sake buɗewa sosai, dan ko a yanzu ka kalleta kasan akwaisu har sunfi na Amima da Ismat ɗin ma dake kusan 27years a duniya. Baƙar fatarta kuwa sai wani sheƙi take da ɗaukar idanun mai kallonta, da gani kasan zatai laushi da sulɓi dan babu ɗigon ƙurji balle tabonsa a fuskata. Kanta ba ɗankwali, hakan ya bayyana gashinta mai yawa duk da kitsone a kanta shiku yama ɗan tsufa.       Maganar da Mammah tai ya sakata sakin Hannun Nabeeha datai sumar tsaye, dan ambaton sunan Nimrah da Mammah tayi sai da taji kamar an kwaɗa mata guduma a saman kai ne, ta wani kafe yarinyar da ido ko ƙyaftawa batayi. Hatta su Ismat sunyi wani irin kasare suna kallon Nimrah, dan harta doke hannun Amima data riƙe mata riga ta baya da alama itama tayi sumar tsaye ne. Dan da gaske fa ƴar yarinyar da bata kai ko sha shida ba ta fisu jikin mata, sai dai su nuna mata shekaru kawai da farar fata. To zama a iya jera masu farin nasu gaban maza ɗari su tsallakesu su zaɓi Nimrah ɗin dake baƙa, dan mazan sun gama zige mata da kalmar fara ko mayyace duk sunbi sun kwaile jikinsu yanzu sun dawo baƙaƙen suke kwashewa sukai gidan aure. (Yo ko mijinki kika biyema da kankare can, tada can, ALLAH sai kin gama wahala da kashe kuɗin da ɗorama kanki ciwuka ƙarshe ya auro wadda bata kaiki komai ba ya sota ya tiritata🤣. Kai mata ku dawo habkalinku, babu biyayya ga abokin halitta akan saɓon UBANGIJI. Wanda ya halicceki ya fiki sanin abinda ya dace dake. Kici abinci mai ƙyau da nagarta kiga yanda zakiyi ƙyau, ba shafe-shafe man gyaran fata da ƙarin haske, ko saka gashi da farce, kankare gira shan supplement na ƙarin baya da gaba, ƙarin girar ido kankare haƙori ke saka mace ƙyau ba. Kiyi ibada, kici abinci mai ƙyau, ki kwantar da hankalinki kiga ƙyau hajjaju, wlhy kyau na asali UBANGIJI kawai ke bada shi ba shirme da sabon ALLAH ba. A duk sanda kika damu da yin ƙyau dan burge mutanen duniya sune zasu taru su zageki da tsine miki kafin zuwa gaban UBANGIJI da kika saɓamawa kika nuna bai iya ba sai ke ƴar iya😏🙄).........✍️[01-16, 11:37] +234 703 449 6321: KIƊA A RUWA 2 39 ........Mammah data fahimci halin da suka shiga da yanda suke kallon Nimrah ɗin sai ta ɗan murmusa, batare da ta sake magana akan abinda ya farun ba ta kama hannun Nimrah tana barin wajen da faɗin, “Bismillah ku ƙaraso ku zauna”.           Sai da suka kalla juna, kafin su bi bayanta jiki a saɓule. Karasowar su falon dai-dai Nimrah da Mammah ke miƙama ruwa alamar tasha na faɗin, “Mammah su waye su?”.        “Sha ruwa”.    Mammah ta faɗa batare data bata amsa ba. Sai da ta tura baki gaba sannan ta amshi ruwan tasha. Ismat dake fatan al'amarin ya tsaya iya haka ta zamo a kujera tana gaishe da Mammah da Ummu da taƙi cewa komai sai mamakin ma ganinsu Ismat ɗin daya cika zuciyarta. Saboda tuna kusan wata ɗaya kenan da kiran Jiddah da sukai akan an hanasu baro Dubai. Da mamaki Nabeeha da su Amima ke kallon Ismat, itako ta fuske dan tasan abinda tai shine dai-dai. Mi Nabeeha ɗin ta gani oho mata, itama sai ta daure ta gaida Mammah kaɗai banda Ummu. Mammah ta amsa mata da kulawa tamkar komai bai faru ba, harda tambayarsu mahaifiyarsu.     Nabeeha ta ce, “Tana lafiya. Mammah dama zamu amshi key ne”.        Ɗan murmushi Mammah tayi da kallon Nabeeha da ƙyau. Ta ƙara ƙyau sosai da ƙiba alamar tana cikin kwanciyar hankali da ƙoshin lafiya. Cike da dattako ta bata amsa da, “Aiko akwai matsala Nabeeha, dan sashen nan naku babu komai a ciki. Tunda za'ai gyara aka fidda komai, abubuwanku masu muhimmanci ne kawai aka bari suna cikin nan sashen ma, amma funichars duk an bada su kuma ba'akai ga zuba wasu ba ganin ba kowa ke zama ba kar aita asara”.      “Amma Mammah da an gaya min kafin a kwashe ɗin, musamman kayan bedroom ɗina dana kitchen dan duk ina buƙatarsu. Gashi na ajiye abubuwa masu muhimmanci da sirrina ne da ya dace ace ni da kaina na ɗaga su a wajen ba wani ba”.        Zuwa yanzu Nimrah ta fahimci wacece a gabata, wato matar Dada data taɓa yankata a cinya, har yanzu tabon na nan kuma. Yanda takema Mammah magana cike da rashin taunawa da girmamawa, yasa zuciyar Nimrah sake zuwa wuya. Hakama Biebah da duk suka fito zuwa yanzu ranta a ɓace ta ƙaraso wajen. Sai dai da ido Mammah tai musu gargaɗi su duka akan kada suce komai. Dan kusan lokaci guda Nimrah da Biebah ɗin suka yunƙuro zasu bata amsa. Babu yanda zasuyi, dan Mammah tafi ƙarfin basu umarni su tsallake.       A karo na farko Ummu tai magana tana kallon su Nabeeha ɗin. “Amma wannan maganar taki babu tarbiyya a ciki, dan ko Adda A'isha bata haifa miki Haysam ba matsayin ƙanwar mahaifinku take Nabeeha. Kayan da kike magana basu suka taɓa miki ba ai Jiddah ce tai komai da ƴan uwanki su Halimatu”.      Rai ɓace Nabeeha ke kallon Ummu, sai dai kafin ta fara maganar da take tattarowa a zuciyarta Ja'afar da suke shigowa shi da Yaya Ma'aruff, Bilal da Ammar ya katseta. “Ummu daina ɓata lokacinki wajen yi mata bayani. Ke Nabeeha kike ko wa? Tashi ki tattara waɗanan tarkacen ku wuce anan.”       Wani mugun kallo Nabeeha ta zuba masa. Ya ɗage gira sama cike da rashin mutunci. Tasan waye Ja'afar dan karonsu babu daɗi. Shi da Ma'aruff shegen zuciya ne da su mai zafi fiye data Dada, kawai dai su suna da barkwanci ne da hira ba kamar shi da baida yawan magana ba. Sannan shi akan jima ba'aga fushinsa ba saboda ya iya shanyewa...         “Malama kina kallona ko akwai magana ne? Nace ku tashi ku bar mana gida..”       “Ni kuma twiny na ƙara mata da gargaɗi na ƙarshe. Kada na sake ganinki a wannan gidan namu, dan baki da sauran hurumin zamansa sai in har Dada ne ya dawo yace ki dawo da kansa. Yanda kika saka ƙafa kika fita da kanki, ki cigaba da zama acan bama buƙatarki a cikinmu. Idan kuma taurin kai yasa kika cigaba da zuwa kina nunama mahaifiyarmu rashin tarbiyyarki, wlhy Ninah da Ruky kaɗai zamu barki da su sai sun saitaki a layi”. Ma'aruff ya ƙare maganar yana nuna mata Nimrah da Ruƙayyan. Aiko ƴar wulaƙancin suka wani tuntsure da dariya Nimrah na faɗin, Received at 4:37 PMReactions:       “Yess Uncle, wlhy ni kaɗai na ishesu su duka ma koba Buddy na. Idan mutum shi ɗan daba ne mai yankan mutane da wuƙa, ni Zakanyar Mammah ce mai kai manyan namun dawa ƙasa harma da ƙananu. Darje baki nake cikin ƙasa, na cikashi da ƙasar taf ta yanda zai iya yima manya magana”.        Ihu Ruky da Bintu da Fiddo suka saka cike da ƙarin haushi suna faɗin, “Naja bomb! Naja bomb! Sai dake Zakanya, Trouble Queen”.        “Mai bombing ɗin ƙananun tantirai ba”. Nimrah ta basu amsa cike da salon iyayi tana wani juya manyan idanunta. Yanzu kam dariya harda su Yaya Ja'afar ɗin, Mammah ta kai mata rankwashi. Tashi tai da gudu tana dariya taje bayan Aunty Biebah ta maƙale. Ummu dake murmushi itama ta ce, “ALLAH ya shirya ku yaran nan. Nimrah dai kin zama Gang leader? Ga mabiya nan irinki kin tara yayunku kuma na ɗaure muku ƙugu. Bari Abban Jiddah yazo aure zance ai muku”.        “Aure Ummu?”.    Suka faɗa a tare suna waro idanu. Asma'u dake dariya tace, “Wlhy Ummu da kin taimake mu, dan yaran nan jinsu suke kamar muma sun girmemu ma”.      Amshewa Halimatu tai da, “Ashe angunan zasu sha shirme da rashin kunya”.          Cike da shagwaɓa suka kalla su Uncle Ma'aruff a tare sukace, “Uncles kun gansu ko? Ai dama sun saka mana ido”.      “Ku barsu sune za'aima aure ba kuba”. Cewar Bilal yana kallon Asma'u ƙasa-ƙasa. Cike da farin ciki suka dawo inda yake suna ma su Asma'u gwalo.       Su Nabeeha sun fahimci fa an ma manta da su a falon gaba ɗaya, yayinda Ismat ta shagala a kallon Ja'afar idanunta cike da ƙwalla. Shi ko ko kallon inda take ma baiyi ba. Bare ma da taga su Aheel sunzo inda suke sai taji wani kishi ya cika mata ƙirji, tana jin inama itace ta haifi su Aheel ɗin.....        _____★              Tunda Adeel ya dawo gidan Yohan baida aiki sai zaman balcony dake facing gate ɗin su Nimrah. Ga alaƙa ta ƙullu tsakaninsa da Ammar a dalilin fita morning jugging. Dan a washe gari saka Yohan yay suka jira har Ammar ya fito a gida, kasancewar sun saba gaisawa normal Ammar ya bama Yohan hannu suka gaisa, sannan ya bama Adeel shima. Daga haka suka fara abinda ya fito da su, suna gudu kaɗan-kaɗan Yohan ke gabatar da Adeel ga Ammar matsayin abokinsa.      Hannu biyu Ammar ya amshesa, haka sukaje suka dawo tare, su suka shiga gida shima ya wuce. Tun daga ranar kuma sai hakan ta cigaba da faruwa, kamar wasa bayan kwana biyu suka haɗu a massalacin anguwar nan ma, tun Ammar baya wani sakin jiki da Adeel bayan gaisuwa harya fara suna ɗan yin hira kaɗan-kaɗan.       Yau ma kamar yanda ya saba yana a balcony ɗin tsaye, gaba ɗaya kuma hankalinsa akan gate ɗin gidan yake. Kunensa da headphone mai shegen ƙyau, sai dai babu tabbacin waƙa yake ji ko wani abun daban. Ganin an buɗe ƙaramar ƙofar gate ɗin ya sa ya ƙara nutsuwa da maida hankalinsa da ƙyau, cikin wata irin bazatar mamaki Nabeeha dake fitowa ta bayyana cikin idanunsa. Da sauri ya cire headphone ɗin daga kunnensa dan tsabar mamaki, ya ciro wayarsa ya shiga camara. Zooming ɗinta yay ta ciki dan gani yake kamar idanunsa ne ke faɗa masa hauka. Itace ɗin kuwa idanunsa ba ƙarya sukai masa ba, dan dai-dai nan Ismat ta fito itama tana waige-waige alamar nemanta take. Ganinta a gefe ta dafe kai da hannu ya sata ƙarasawa inda take da sauri, sai dai baya jin mi take ce mata har aka wangale gate ɗin duka mota ta fito. Dai-dai inda su Nabeeha suke Rayhana tai parking, buɗe motar da fitowar da sukai ita da Amima suma suka nufi su Nabeehan ya sake cire masa tantama. Sai ma ya rasa abin cewa shi kam. Yana anan tsaye tamkar wani gunki Yohan daya fito ya kai dubansa inda yake kallo, bai san su waye matan ba, dan haka ya juyo ya kallesa tare da faɗin, “Sir ka sansu ne?”.          Shiru kamar Adeel bazai tanka ba sai kuma ya ce, “Ba saninsu bane mai muhimmanci, sanin alaƙarsu da wannan gidan. Zaka iya bincika min”. Received at 4:37 PM       “Nima irin wannan tunanin naki na zomin a rai. Musamman dana fahimci ba tayi wani serious bane kan batun sai ma zancen ƙulla auren da suke sonyi tsakanin ƴar su da ɗan shugaban kasa. Duk da yaron ya nuna ba sonta yake ba sun nace.”       “Kinji ba! Ai halin ɗan Adam sai shi wlhy.”      Da wannan zantukan suka fice a gidan batare da sunma yaran nasu sallama ba. Sai fitar motarsu sukaji a gidan. Da wannan damar Ismat tai amfani ta fito itama tabar gidan da kaya niƙi-niƙi. Sai dai maigadi ta saka ya tare mata taxi a waje bata ɗauki motar kowa ba. Dan dama dai Mamansu da Aunty Mamawo da Nabeeha keda mota kawai a gida. Su basu da ita...... ================      Anan gidan Mammah bayan tafiyar su Nabeeha Malam Almu ya kawo ƙaninsa ciki dan su gaishe da Mammah su mata barka da dawowa. Da fara'a kuwa ta tarbe su. Tare da amsa musu gaisuwa da kulawa tana tambayar Malam Almu mai jiki. Kamar yanda yay ma malam Buba bayani itama haka yay mata duk su Yaya Ma'aruff na jinsa. Ya kuma nuna ƙaninsa Sanda ya musu bayani a kansa da aiki da ya fito nema idan ya samu. Sai dai bai nuna anan gidan ba kamar yanda suka shirya.      Cikin sa'a kuwa Mammah ta ce, “To ai bai kamata yay nesa da kai ba ko Malam Almu. Sai a bincika anan idan da wani aikin sai ya dinga yi, kaga sai kuyi zamanku ka samu abokin hirar dare tunda shi driver ba kwana yake ba yana tafiya gida da yamma”.          “Nagode Hajiya Mama, ALLAH ya saka da alkairi ya ƙara lafiya da nisan kwana mai amfani. Sanda kayi godiya mana”.     Godiyar Sanda ya fara shima kamar yanda yaga malam Almu nayi, suka juya suna sake godiya gasu Yaya Ma'aruff suma. Sai da Mammah tace ya isa sannan sukai shiru. Daga haka ta ɗan yima Sanda tambayoyi yana bata amsa. Kai ta dinga jininawa cike da nazarin al'amarinsa, kafin ta sallamesu su koma bakin aikinsu...     Suna fita Yaya Ammar ya ce, “Mammah wai baƙya jin tsoron ɗauke-ɗauken nan kada wataran mu ɗauki abinda zai dame mu. Yanzu fa akan al'amarin Dada kowa zai iya shigowa jikinmu dan ya cutar damu. Shiyyasa kikaga ma Yaya Imran kullum yana kaffa-kaffa”.         “Hummm Ammar kenan, banda abinka bawa na iya gujema ƙaddararsa daman? Duk abinda kaga ya faru hukuncine na UBANGIJI. Jarabawa ba tawaya bace. Ba kuma faɗuwa bace ga bayi, sau tari kankarewar zunubi ce ko tsanin nasara daga wata ɗaukaka da UBANGIJI zai kai bawa kanta. Kar ku damu da makircin masu makirci, idan duk wanda ke zagaye da kai mugune mai fuska biyu, in har ka tsaida gaskiya, kai ka zauna da shi da kyakkyawar zuciya bisa umarnin ALLAH, wlhy ko shine ibilis akan sheɗanci da mugunta sai dai yayi ya barka. Dan shi bai isa canja komai daga ƙaddararka ba koda murmushi fuskarka ne, sai dai yayta wahalar banza da ɓata lokacinsa akan ka amma ko badaɗe ko ba jima saika cimma wannan nasarar. Ƙilama UBANGIJI yay masa tsahon ran da zai koma neman taimakon ka. Kudai kuyi addu'a kawai, idan ma da manufa mutum yazo mana, ALLAH zai hanashi nasarar cutar damu. Shima da yake can ALLAH zai kuɓutar da shi idan lokaci yayi, dan bana yanke ƙauna da rahamar UBANGIJI akan Muhammad zai fito ya dawo garemu. Ban taɓa jin na sare akan wannan fatan ba, duk da ina jin tsoron kar su cutar mana da shi. Amma ALLAH na tare ta shi, addu'a ta da taku na tare da shi. In sha ALLAHU indai gaskiyarsa ce ta kaisa wancan wajen komai tsahon lokaci zata ƙwatoshi daga hannun azzaluman makirai...”        “In sha ALLAHU Mammah”.    Suka faɗa a raunane, Biebah da Ammar kuwa sai da suka share hawaye. Su Ja'afar dai idanun sun canja launi amma babu hawayen. Su Nimrah dake laɓe suna sauraren su suma dai duk jikinsu yayi sanyi. Cikin Zuciya Nimrah ke jin tana son sanin inda Dadan yake? Miya faru da shi? Mi ake ɓoye musu game da shi?. A zahiri kam batace komai ba ta nufi komawa ɗakinsu, sauran duk suka bita dan dama tun shigowar maigadi Mammah tace su koma ɗaki abinsu. Shine suka laɓe, da farko dariyar shigar ƙanin Maigadi suka maƙe sukeyi, dan yayi wani shigar gayun ƙauye irin masu iyayin nan ne abin dariya...... •••••••••••••••••••••••••••••• ★ONE WEEK LATER★         ★10:15 AM★ SECRET MEDICAL BASE Received at 4:37 PM        “Colonel Imran… mun kammala dukkan gwaje-gwajen da muka yi masa.” Dr. Idris Ali, ya faɗa yana ɗan gyara gilashinsa.         Imran bai ce komai ba. Ɗaga masa kai yay alamar ya ci gaba.     Doctor ya jinjina kansa, kafin ya buɗe baki ya cigaba da faɗin, “Mu godema ALLAH jikinsa ya nuna ƙarfin juriya mai ban mamaki. Idan ba haka ba, da gubar da aka saka masa ta riga ta yi mummunan tasiri a lafiyarsa zuwa yanzu.”      Cikin wani irin bugawar kai Faro ya ɗan matsa gaba, murya ƙasa-ƙasa da alamar tashin hankali a ciki ya furta, “Guba kuma Doctor?”.      Dr. Idris ya ɗan numfasa, kamar yana neman kalmar da zai musu bayani da ita da bazata ɗaga musu hankali ba fiye da kima. “Eh. Poisoning ne… dan abinda sakamakon bincikenmu ya nuna mana kwanaki uku kenan shiyyasa ma muka sake masa sabon gwaje-gwaje akan hakan, kusan wannan dalilin ne ya hanamu faɗa muku komai a ranar wednesday data gabata mukace ku saurare mu. Sai dai ku kwantar da hankalinku poising ɗin bai jima da fara shigarsa ba, da dai ya jima a inda yake ne zai cigaba da shiga kamar yanda koma su waye suka tsara, sanan zai dinga tasiri a jikin nasa ne a hankali har sai ya gama yima jikinsa illa ne zai bayyana. Dan haka ko a yanzu babu wani damuwa mai girma. Sai dai idan aka bar shi haka a jikinsa, akwai haɗari sosai anan gaba”.        Imran da gaba ɗaya yake jin jinin jikinsa na tsiyayewa tamkar an ɓula ledar ruwa da tsinin allura ya rumtse idanu yana matse hannunsa.........✍️ Received [01-16, 11:37] +234 703 449 6321: KIƊA A RUWA 2 40 .........Gaba ɗaya ran Hajiya Hasiba a dagule yake. Koda su Nabeeha suka koma gida da nasu ɓacin ran sun sameta tana faman kai-kawo a falo. Aunty Mamawo zaune itama ta rabga tagumi. Ismat ce kawai tai ƙarfin halin tambayar su ko lafiya? Amima da Rayhana kam da ƙorafin abinda ya faru suka fara. Nabeeha dai ranta a ɓace yake, dan haka bata tankama kowa ba ta wuce upstairs abinta. Dan a wannan gaɓar ta gama yarda dole ta nemawa kanta mafita. Mafitar kuma ɗaya ce jal shine komawa gidan su Haysam. Dan a can ne kawai zata samu damar maganin wannan shegiyar mayyar yarinyar da ganinta ya gama birkita mata dukkan lissafinta, sannan ta samu mafakar gujema Adeel da bata san manufarsa ta biyosu ƙasar nan ba.      Tsakanin Aunty Mamawo da Hajiya Hasiba babu wanda ya kula tambayar Ismat, sai ma umarnin su wuce ciki da Mamawo ta basu. Hakan ya sake tabbatar musu babu lafiya. Wucewar sukai, dan sun san halinta da masifarta bata musu ta wasa. Shiyyasa ma suka fi son Hajiya Hasiba dan tafita sauƙin kai. Koda suka hauro saman ma kowa inda yafi masa ya nufa, dan kowa da abinda ke ransa da zuciyarsa. Ismat dai a wannan gaɓar ta gama yanke shawarar komawa gidan mahaifinsu. Dan tayi alƙawarin bazata sake komawa Dubai zama ba sai inda ziyara itama tare da mijinta Yaya Ja'afar in sha ALLAHU. Dan a wannan karon yaƙi zatai ɗan gaske babu gudu babu ja da baya. Ta share ƙananun hawayen da suka cika mata ido, wani irin wutar sonsa na sake ruruwa mata a zuciya, saboda ganinsa ba ƙaramin tayar mata hankali yayi ba. Ya ƙara ƙyau da cikar jiki da buɗewa irin ta magidantan dake samun dukkan gata a wajen iyalansu. Tunda yay auren nan bata yarda taga matarsa ba saboda bata buƙatar hakan, amma a yau tana jin kwaɗayin ganin Shariffa ɗin duk da ta santa dama can.        Akwatin kayan da tazo dasu daga Dubai ta buɗe, kasancewar ƙaton gaske ne dama kuma ta haɗo komai nata mai muhimmanci daga can sai ta sake tattare na nan gidan ma ta loda a ciki, ganin ya cika da yawa ta sake ɗaukar wani ƙarami ta zuba sauran abinda ya rage ta rufesu. Bakin gado takai zaune ta ɗauki wayarta ta fara kiran Aunty Jiddah. Gidanta take son fara zuwa, dan tai mata rakkiya gidan Abban.       Da mamaki Aunty Jiddah data ɗaga wayar ta ce, “Yaushe ke kuma a gari haka?”.       “Aunty mun jima da zuwa. Kina gida ne dan ALLAH?”.      “A'a ina gidan Aunty Fateema, zata aurar da ƴarta Aminatu muna shirye-shirye dan za'a fara gobe idan ALLAH ya kaimu.”          “ALLAH ya sanya alkairi, yaushe zaki koma?”.      “Amin ya rabbi. Lafiya kuwa?”.   “Aunty zan zo ne, ni dai yaushe zaki koma?”.      “Ki tafi kawai ai yara na nan, Shafa'atu ƙanwarsa ma na gidan tazo weekend”.        “Okay tom. Ki gaida Aunty Fateeman, in sha ALLAHU dani za'ai kamun gobe”.      Daga haka ta yanke wayar tabar Jiddah da mamakinta....      ★ Anan falo kam bayan wucewarsu Aunty Mamawo ta furzar da iska mai zafi tana kallon Hajiya Hasiba. Ta ce, “Aunty tunani ko damuwa bazata kaimu ko ina ba. Kawai muje wajen wani mutimina, shima yana ƙoƙari ya iya aiki, da rafanai yake aiki na tabbata zai mana nasa ƙoƙari kafin muje India ɗin. Dan dole gaskiya muyi wani motsi a wannan gaɓar, dan ina ji a jikina shirun Adeel bazai zama alkairi ba”.          “Kina ganin zamu samu mafita kuma?”.       “Tabbas Aunty, dan na yarda da aikin Malam Ƙolo sosai”.     “To shike nan muje ai kawai mi zamu jira. Dan mutumin nan na tabbatar shima yana can ya bazama hanyar samun damar ganin Haysam, dan gaskiyarki kam shirunsa bazai zama alkairi ba.”          “Wlhy ni wannan bai dameni ba Aunty, idan ma ya saka an kashe shi matsalarsu ce. Miye amfanin wani Haysam a rayuwar Nabeeha, banda soyayyar wahala da take masa ma. Garama ya kashesa ta samu wanda ya fisa koda ace zata bar Adeel ne, idan ma babu wata illar da ita First lady ɗin ta ambata ba shike nan ba. Dan ni ban yarda ma da matar ba kin san dai mutane da baƙar hassadar tsiya a wannan zamanin. Kowa yafi son ace shi shine kai kana ƙasanshi kana masa bauta bare ma manyan ƙasar nan”.       “Mizai hana nayi hakan”.   “Yanzu yanzu fa. Ko zaka kira abokinka ne Ammar?”.       “Kodai kayi haƙuri zuwa anjima, kuma ba Ammar ya kamata a tambaya ba dan kar ya zargi wani abun tunda mun samu ya fara sakin jiki damu.”            Ji Adeel yay kamar yace bai yarda ba, amma sai ya daure dan baya son Yohan yaga zalamarsa a fili da yawa, har ya kawo masa raini dan har yanzu bai san shi ɗin waye ba. Kuma baya son ya sani har ya gama abinda ya kawo shi ya bar ƙasar nan. Duk da yau da safe yaga saƙon Ummu ɗinsa ta Email akan tana son ganinsa da gaggawa, ya tabbatar koma miye take nemansa a kansa ba na wasa bane. Kuma dole ya amsa wannan kiran dan baya tsallake maganar iyayensa.....       Bai sake magana ba sai ma barin wajen da yayi ya koma kan kujerar da take a balcony ɗin ya zauna zuciyarsa fal abubuwa. Dan gaba ɗaya yarinyar can ta rikita masa lissafi ko zancen abinda ya kawo shi ƙasar nan bai sake waiwaye ba. Kai su kansu su Hajiya Hasiba ɗin tunda suka iso bai bi takansu ba, sai ma da yaga Nabeeha yanzu ya tuna da al'amarinsu...........✍️KIƊA A RUWA 2 41 ........Da ƙyar Daddy Imran ya iya fisgo kalma ɗaya wajen furta, “Wace irin guba ce?”. “Slow-acting toxin. An tsara ta ne don ta lalata jiki a hankali ba kashewa nan take ba. Hakan na nuna wanda ya aikata ya so yaga yana rayuwa cikin rauni ne.” Shiru ɗakin yay dan kowa da kalar da raɗaɗin da zuciyarsa ke masa akan jin wannan baƙon al'amari mai rikita lissafi. Suna cikin farin cikin babu wani damuwa a tare da Dada a kwaje-kwajen farko, ashe tashin hankalin na gaba. Da ƙyar Faro ya yanke shirun nasu. “Doctor yanzu minene mafita? Tana da makari ne?”. Doctor ya ɗan gyaɗa kansa. “Tabbas za'a iya samun makarinta, abin da ya rage mana shi ne inda zamu same sa, musamman a ƙasar nan tamu kuma da bana jin zamu samu ɗin kai tsaye, idan ma mun samu hankalinmu bazai kwanta ba ga duk wanda zai bamun. Dan duk wanda ya samar da gubar dama dole shine mai makarinta. A yanzu kuma mu kowa ba abin yarda bane a wajenmu. Musamman tunda bamu san wanda ya aikata masa haka ba. Sai dai mubi wata hanyar sirri da cikakken tsaron da zamu fitar da ita gaba ɗaya.” Imran ya ɗago kansa ya zuba masa idanunsa da suka juye jazur. Kai tsaye ya furta, “Waje ke nan?” “Tabbad Sir! Asibiti na musamman a waje ya kamata mu kaishi. Zaman wata ɗaya zuwa biyu. Idan aka yi hakan da wuri zamu tsare rayuwarsa da cikakkiyar lafiya.” Komai Imran bai sake cewa ba, sai ma ya tashi tsaye a hankali, sai dai nauyin abin da yake ji ya kasa ɓoyuwa akan fuskarsa da kuzarin jikinsa. Ɗan juyowa yay ya kalla Doctor ɗin, cike da gargaɗi ya furta, “Babu wanda zai san wannan bayan mu ukun nan.” Dr. Idris ya gyaɗa kai da girmamawa. “Mun riga mun ɗauki rantsuwar sirri ai Sir.” Imran ya juyo ga Faro, idanuwansu suka haɗu a waje guda. “Zan sanar da shugaban ƙasa yanzu.” Faro ya ɗan murmusa da gyaɗa kansa, sai dai murmushin da ke ɓoye fushi. “Ka sanar da shi. Amma ka faɗa masa gaskiya ɗaya: Zak-Shadow bai fito daga prison don ya mutu a asibiti ba.” Imran ya gyaɗa kansa yana ɗaukar wayarsa, harya fara tafiya ya tsaya a ƙofar ɗakin, a taƙaice ya furta “Ba zai mutu ba in sha ALLAHU.” daga haka ya fice ya bar Faro da Doctor Idris na cigaba da tattaunawa. Dada da basu san duk ya gama jin abinda basa son yajin ba ya bar jikin ƙofar yana murmurshi. Drip da ake faman saka masa a kwanakin nan dama doctor ɗin ya saka masa bayan sallar isha'i, shine ya saka shi barci har su Imran ɗin suka shigo gidan bai sani ba. Yanzu ma ya farka ne sai yaga ruwan ya ƙare ya cire da kansa, ruwa da yake buƙata na sha daya duba babu a ɗakin ya saka shi ƙoƙarin fitowa duba Dr Idris ɗin, dan koda yaushe Doctor na tare da shi a gidan. Barin wajen yay ya koma ya zauna a bakin gado. A zuciyarsa yana faman maimaita kalmar poising ɗin, sai dai fuskarsa da murmurshi, dan ya jima da fahimtar hakan a tare da shi, musamman a watannin nan da suka gabata. Har ma yana tunanin yaushe hakan ta faru? Tun yana a prison ɗin, dolene a ɗayan biyu gubar ta shigesa. Mafi ƙarfi a zuciyarsa shine television da aka kawo ɗakinsa watannin da suka wuce, ko kuma ta hanyar securitys ɗinsa...... %★%★%★%★% A ɓangaren su Hajiya Hasiba kam abinda suka jiyo ga bokan Mamawo ya matukar rikitasu, amma sai Hajiya Hasiba tace ita dai su sake zuwa wajen wani mana. Ko suje India ɗin kona kwana biyu ne. Mamawo ta yarda da shawarar, amma tace su fara fuskantar Adeel. Itama Hajiya Hasiba bata musa batun ba, sai dai sun nema ganin Adeel ɗin shi kuma ya toshe hakan. Dan yama ɓoyema ganinsu gaba ɗaya dan haka dole sukai hakuri dan zuciyarsu na kitsa musu ko wani abu yake shiryawa. Ga First lady ta takurama Hajiya Hasiba akan harkokin bikin ƴarta, dole ta haƙura da batun India ɗin ta maida hankali a kanta. Har takai ma bata fahimci Ismat bata gida ba sai bayan kwana biyu. Sai dai tana taɓota tace tana gidan Aunty Jiddah zatai kwana biyu sai ta saki batun ta. Dan bata kawo a ranta wani abu Ismat ɗin ke shiryawa na komawa gidan babansu ba. Received at 2:37 PM Ita ko Nabeeha tunda suka baro gidan Mammah a waccan ranar al'amarin Nimrah ta ɗauka ta saka a zuciyarta dan girman yarinyar ya tayar mata da hankali matuƙa. Tun tana ɗaukarsa ƙaramin abu har yake neman zame mata ciwo a kwanakin gaba ɗaya bata jin daɗin ranta dama jikinta duka. Babu abinda take saƙawa sai yanda zatai da Nimrah. Wannan ya ɗauke hankalinta itama bata shiga sabgar kowa da komai na gidan. Su kuma su Amima holewarsu suke hankali kwance da yawon tsiya ita da Rayhana kullum. Dan uwarsu ta tsaya musu..... <<%>><<%>><<%>> “Waye shi wannan?”. “Wani yaro ne malamin islamiyyar su. Gaba ɗaya alamominsa sun nuna sonta yake yi. Dan haka da shi ya dace muyi amfani wajen yi mana wannan aikin. Saboda gidan tako ina zagaye yake da ƙyamarorin zamanin nan. Sannan kamar yanda na sanar maka ranar da gaske sun mantar da ita asalinta, su kaɗai take ma kallon iyaye a yanzu.” “Da gaske mutanen nan shu'umai ne fa Mole, wannan halayyar a jininsu take ba Zak-Shadow ɗin bane kawai shege”. “Zan tabbatar musu mun fisu shu'umci, ba laifinsu bane kuma. Laifin Hafsatu ne data ɗaukar min yarinya ta bashi. Kuma ta godema ALLAH data mutu, dan da ace tana raye har yanzu, sai na ɗanɗana mata fiye da abinda take tsammani na azaba a tafin hannunta duk da son da nake mata”.. “Mole manta kawai, wauta ce irin ta mata da zigar ubanta. Ba gashi sun kuma ɗanɗana daga hukuncinmu ba yanzu sai labarinsu. Yanzu shi wannan yaron mai gemu kamar jelar tsatso ya za'ai yazo hannun mu? Dan su Oga sun ce muyi faka-faka babu ɓata lokaci muna buƙar yarinyar mu Nimrah tai mana aikin nan da gaggawa ta dawo hannumu.” “Karka damu wannan duk mai sauƙi ne. Dan tana nan da halin nan nata dana santa da shi har yanzu. Na tabbatar idan taga videon nan kodan son da takema uwarta zata dawo hankalinta. Ballema idanunta ya sake buɗewa yanzu tayi karatu. Kamar yanda kace babu ɓata lokaci kawai saƙon nan na farko ya dace ya fara riskarta, dan yaran ya sanar min watannin baya ya aika mata ƙyautar litattafai, kaga sai muyi amfani da wannan damar nake ga ko.” “Hakan yayi, zan saka a cikin satin nan a sace min yaron. Amma fa kaima sai ka sake kula gaskiya. Dan Imran ɗin nan na tabbatar shegen kansa ne zuwa yanzu. Duk da dai a zahiri baya wani abu da zai tada mana hankali, ina jin tsoron shiru-shirun sa”. “Ni ko kaga bana wani tunani mai girma a kansa, saboda uban ƴan taurin kan can shi ne ƙarfinsa, rashin sa a kusa da shi kuma duk ya sake rage masa kuzari.” “Kai ma kayi magana ta gaskiya. Amma duk da haka kada mu sakankance. Bari naje dan asuba ta gabato. Sai na jika”. Sunyi sallama Dagger ya bar gidan, dan gida ne dama na haya mai mutane da yawa Mole yazo ya kama ɗaki. A yanda yake kuma baka isa kace yana da wata suffa ta mutanen banza ba. Tsabar iya taku ma jama'ar gidan da sunan Malam suke kiransa...... <<<<<✷⁠‿⁠✷>>>>> A gidan Mammah kam yau su Nimrah gidan Daddy Imran suka tafi zasu kwana. Harda Feddo da Bintu kuma suka shirya weekend ɗin nasu. Uncle Bilal ne ya kaisu da kansa, dan dama su ƴan gatansa ne. Tunda suka iso suka cika gidan da hayaniyarsu da karaɗi, aka fara faɗan ƙa'ida tsakanin Ruky, Nimrah da auta da suke kira Lolo. Dan shine sakon Ruky, dan haka yake ganin itama Nimrah sakon tashi ce. Wani lokacin kuma suke jansa tsiyar, dan ko yau suna shigowa ɗakinsa suka wuce suka kwaso masa chocolates na makaranta suka hau ci. Shi ko yana dawowa daga Islamiyya aka fara, sai da Ammie ta shiga tsakani. Sun gama da Lolo suka koma kan Aunty Ma'u. Wai sai ta faɗa musu miye tsakaninta da Uncle Billa. Cike da baƙar magana tace su shaƙeta ta sanar musu to. Da yake shaƙiyay ne suka sakata a gaba wai ai sun sani, Fiddo harda cewa ai taga wani bangle a ɗakin Uncle Billa an saka sunan Aunty Asma'u ɗin. Received at 2:37 PMReactions: Duk abinda suke Ammie na jinsu, itama kuma hirar tasu ta fara kai hankalinta akan al'amarin Asma'u ɗin da Bilal, dan kwan biyun nan ta fahimci ko yaushe Asma'u na maƙale da waya, idan ta tambayeta sai tace wai assignment take yi. Ashe ita ta maida assignment ɗin. Kai yaran yanzu sai a barsu dai kawai. Tai murmushi mai yalwa, dan har cikin ranta wannan haɗin ya mata. Wlhy idan duk ƴaƴan data haifa zasu kasance matane ace yaran gidan Mammah suka auresu zatafi kowa farin ciki, dan jinin Mammah jinin alkairi ne. Abotar Imran da Haysam babban rahama ce kuma alkairi ga zuri'arsu guda biyu. Addu'ar fatan alkaici tayi ta cigaba da sabgarta.........✍️ Received atKIƊA A RUWA 2 42 ........Bayan la'asar su Nimrah suna a garden suna basket ball su duka huɗu sai Yaya Khalifa, Yaya Mu'azz da Yaya Imam da suka zo gidan babu jimawa, sai Auta Lolo. An raba team ɗin biyu, amma Nimrah da Ruky sunƙi yarda a rabasu, dan haka sai ƙwange sukema su Mu'azz da rinto.         A yanzu ma ana tsaka da gardama Nimrah da Ruky sun dage kuma akan rinto ne Khalifa ya hararesu da faɗin, “Kufa matsalar ku rinton jaraba, shiyyasa sam bana son haɗa sabga da Ninah da Ruky munafukan yara ne ALLAH”.         “Ashe ka gane Broth, wlhy haka suke”. Cewar Mu'azz shima yana hararsu. Baki Ruky da Nimrah suka taɓe, Nimrah zatai magana sallamar maigadi ta dakatar da su. Imam ne ya amsa masa duk suka juyawa suna kallonsa. Kai tsaye inda Nimrah take ya isa, ya miƙa mata ƙaramar ledar hannunsa yana faɗin, “Saƙo ne wani ya kawo wai a baki. Yace malamin ku ne na islamiyya Kamal”.      Tsit wajen yay ana kallan kallo, sai Bintu ce da tai dariya da faɗin, “Humm guy ɗin nan fa ya dage wlhy”.        Kafin wani ya bata amsa Lolo ya amshi ledar, maigadi ya juya abinda yabar wajen. Dai-dai Lolo na fiddo littatafan cikin ledar. Yanzu kam dariya Feedo, Ruky, Bintu suka kwashe da shi. Yayinda Nimrah taja tsaki. Aunty Asma'u kuma ta tambayesu waye ya kawo?. Labari su Feedo suka bata, har su Mu'azz duk na saurarensu, sai dai abin mamaki duk fuskokinsu sun canja, dan cikin faɗa Khalifa ya ce, “Zamu ci uwar guy ɗin nan kuwa, ƙannenmu da aka tura makaranta ne abin bibiyarsu da soyayya? Dan ubansa aure akace za'ai musu?”.       Cikin ɓacin rai Imam ya ce, “Dolene muje har makaranta muja masa gargaɗi kam, wannan ai rashin hankali ne”.      Mu'azz kam daya kume bai iya ya tanka ba, dan fuuu yabar garden ɗin ma. Khalifa da Imam suka take masa baya. Daga haka wasan ya watse. Ammie dake falo sai ganinsu tai suna shigowa ɗai-ɗai. Bata ce da su komai ba dan tana waya da Daddy Imran ne....        Washe gari daga Nimrah har ƙawayenta babu wanda ya sake bin batun litattafan Sayyadi Kamal kamar wancan karo da suka ma barsu a gidan Aunty Mimi. Dan tunda suka tashi ma suka taya masu aiki gyaran gidan da haɗa breakfast. Bayan sun karya kuma sukai shiri wucewa gidan Baffa dan Hajiyar Daddy Imran ta dawo daga ƙauye jiya da yamma. Tunda Aunty Asma'u ta sanar musu sukace yau can zasu yini. Duk da Ammie na son su zauna babu yanda ta iya. Dole ta haɗa lafiyyayen farfesu da kunun aya da kunun gyaɗa tace su kaima Baffah da Hajiyar (Iyayen Imran kenan). Nimrah ce ƙarshen fitowa a ɗakin. Ta kammala rolling veil ɗin abayarta kalar maroon da adon milk da taji stone tana maida kayan kwalliyarsu a make-up kit ɗinsu idanunta suka sauka akan books ɗin Sayyidi Kamal dake zube a side drawer inda tun jiya Bintu ta zube su. Samun kanta tai da ƙarasawa inda suke ta ɗaukesu su duka uku yau dai tana kallo. Zuuu taɗan buɗesu a tare, sai ga wata ƴar ƙaramar takarda ta faɗo a ɗaya daga cikinsu. Takardar tabi da kallo, ganin rubutun jikinta ta kai duƙe ta ɗauka.        _Ba litattafan bane muhimmanci a gareki yau kamar saƙon farko, ainahin saƙon yana a littafi mai jan bango shafi na hamsin da uku da shafi na tamanin, ki tabbatar ke kaɗai kikaga abinda ke ciki batare da kowa ba har aminiyarki, saboda muhimmancin abinda ke ciki da zai amfaneki ke kaɗai. Idan kuma kika bari wani ya gani bayan ke to tabbas zai mutu._      Takardar ta ɗan jujjuya cike da mamaki zuciyarta na wani kalar bugawa da sauri-sauri saboda kalaman ƙarshe, dai-dai nan akai knocking ƙofar ana kiran sunanta. Dan haka ta maida takardar kawai cikin littafin farko tana amsawa da haɗiye abinda ke shirin hargitsa mata brain, sai kuma ta buɗe handbag ɗinta ta saka duka books ɗin a ciki dan basu da wani girma sosai. Haka ta fito zuciyarta na kai-kawo akan abinda ta karanta. Amma da yake tana da wayo sai ta danne ta yanda kowa bazai fahimta ba. Received at 2:38     Yau kam Yaya Khalifa ne ya kwashe su zuwa can gidan Baffan. Cike da farin ciki suka zagaye nutsatstsiyar tsohuwar mai cike da kwarjinin ibada da lafiyar data haɗu da jin daɗin rayuwa. Hajjo tsohuwa mai ran ƙarfe kenan, mahaifiya gasu Imran da a yanzu ta zama uwa harga su Mammah, sannan kaka gasu Nimrah. Dan dattakonta yasa itama bata san raba ɗaya biyu ba, ta zama ginshiƙin dunƙule familyn nan uku da basu da alaƙar jini a yanzu sunfi ma waɗanda keda alaƙar jinin gina ƙyaƙyƙyawan zuminci...          “Oh ni Bilkisu, yaran nan ina zakuje da girman jiki? Ba'a kauda uwarku Biebah ba balle yayunku amma neman dannesu kuke da girman jikin ku, anya bazance a haɗeku rana ɗaya da Habibah da su Asma'u ba”.      A tare suka gwalalo mata idanu, cike da shagwaɓa har suna haɗa baki wajen faɗin a'a gaskiya su auren su sai sannan da shekara goma.       “Shekara goma? Kuji min shaƙiyan yara, sannan kuma in sha ALLAHU ai sai dai lissafin auren ƴaƴanku. Ni yanzu kunga tunda gaku ku duka huɗun yau ba lalaci da surutu zaku yimin ba. Tashi zakuyi kumin kwalemar ɗaki a fitar da komai a canja min jere na, dama su Asma'u zance suzo suyi, amma tunda gaku shike nan sun huta”.        A tare suka amsa mata da to. Sai kuma Nimrah da duk bata da kuzari ta ce, “Granny ina Baffa wai?”.       “Naja'atu sun fita shi da baban ku Ammar, dan kamar ma suna can gidan kakanku Nasiru. Amma nasan anjima kaɗan zasu dawo”.             Kai Nimrah ta jinjina, har sun miƙe Hajjo dake binta da kallo ta kira sunanta, juyowa tai, sai kuma ta tako inda Hajjon take. Sai da ta kama hannunta ta zaunar kusa da ita sannan taima su Fiddo da suka tsaya suna kallonsu alamar suje su. Basuyi musu ba suka wuce hanyar bedroom ɗinta. Ita kuma ta maida hankalinta ga Nimrah.        “Naja'atu mike damun ki? Ko baki da lafiya ne?”.     Sai da gaban Nimrah ya faɗi, dan bata taɓa zaton wani zai gane halin da take ciki ba. Amma sai tai ma Hajjo murmushi da girgiza kanta. “Ba komai Granny, mi kika gani?”.         Hajjo dake kallonta cike da nazari ta ce, “Ban yarda ba Naja'atu, nafa san halin kowa a cikinku, ko yaya kuka canja kuma ina ganewa.”       Har Nimrah ta buɗe baki zatai mata bayanin abinda ta gani a takardar nan sai kuma ta tuna kalaman ƙarshe na cewar duk wanda ta bari ya sani zai mutu, da sauri ta canja zancen tana kwantar da kanta jikin Hajjo ɗin. “Granny da gaske ba komai. Kawai dai yau na tashi ne duk zuciyata wani iri ba daɗi, kuma gabana nata faɗuwa”.      Ajiyar zuciya Hajjo ta saki a hankali, sai kuma ta shafa kan Nimrah ɗin cike da lallashi da so da ƙauna ta ce, “Ki yawaita ambaton Hasbunalahu wani'imal wakil da talatin ANNABI kinji. In sha ALLAHU babu abinda zai faru sai alkairi. Barsu ma suyi aikin muyi hirar mu”.        “Granny zan taya su ina son nima nayi. Amma kin zo mana da farar mu?”.     “Buhu guda ma kuwa, tana nan a store dama in baku zo yau ba zan bayar a kai muku, damma na manta ne da A'isha tazo ɗazun ita da Bilalu ban basu ba”.     Farin ciki sosai ya bayyana a fuskar Nimrah, sai kawai ta nufi ɗakin Hajjo tana ƙwalama su Ruky kira. Da kallo Hajjo ta bita tana murmushi, dan har cikin ranta take ƙauna da tausayin Nimrah....... <•><•><•><•><•><•><•> ★ SECRET MEDICAL BASE ★              Yanda Imran yake a ruɗe ko damuwa da kallon lokaci baiyi ba ya dannama shugaban ƙasa kira. Cikin sa'a kuwa ba a jima ba aka amsa. Sai da ya sauke ajiyar zuciya mai nauyi kafin yay sallama. Daga can shugaban ƙasa da alamu ya nuna barci yake ya amsa, duk da dai a cikin murya mai nutsuwa ne.         “Imran.”      “Ranka ya daɗe ka gafarce ni na tashe ka a barci bazan iya haƙuri bane shiyyasa ko lokaci ban damu da dubawa ba na kira ka.”        “Karka damu Imran nima barcin ya ɗauke ni ne kawai batare da na shirya masa ba. Nima ina son kiran naka a daren nan ai. Amma minene ya tada maka hankali haka?”. Received at 2:38 PM      Shiru kaɗan ya biyo baya Imran ya gagara magana saboda abinda ya toshe masa maƙoshi. Shima sai Shugaban ƙasa bai iya yace komai ba yana dai saurarensa cikin shiru, irin shiru na masu fahimtar juna ba tare da doguwar magana ba. Tsohon minti guda Janar ya katse shi da faɗin,       “Ka samu abin da ka je nema ne Imran?”    Imran ya sauke numfashi karo na farko a hankali. Muryarsa da ɗaci ya furta, “Eh, ranka ya daɗe. Amma abin ya fi yadda muke zato nauyi.”        “Faɗa min kawai”.    “Akwai guba a jikinsa. Ba ta gaggawa ba, amma an tsara ta ne don ta lalata shi a hankali. Likitoci sun tabbatar da cewa a nan ba za a iya magance ta gaba ɗaya ba, koda akwai makarinta zai iya kasancewa a hannun wanda sukai aikin yake ko suna da alaƙa da wanda suka yin, dan dole mai makarin shike da gubar. Fitar mu nemata zai basu ƙofar sanin sirrinmu”.       Shiru ne ya sake biyo bayan bayanin Imran ɗin. Dan Janar ya kasa koda motsin kirki tsabar yanda zancen ya buge shi shima. Imran ya san wannan shirun na Janar shiru ne na mutum da ke ƙoƙarin riƙe fushinsa  shima, dan dole Janar zai ji kamar yanda suka ji a lokacin da Doctor ke sanar musu.       “A wajen akwai maganin? ta hanyar da muke buƙata?”.     Janar ya faɗa cikin wata irin murya mai bayyana ɗaci da zafi.       Amsa Imran ya bashi, “Akwai, ranka ya daɗe. Amma zai iya ɗaukar wata ɗaya zuwa biyu inji Doctor.”        Muryar Janar ta sauya kaɗan zuwa matsayin shugaban ƙasa, cikin nauyin umarni ya furta. “Amincewar UBANGIJI kawai muke nema. Amma babu wanda zai ji wannan har Haysam.”      “Mun riga mun kulle komai Sir.” “Zan zo yanzu. Ina son na gansa.” Imran bai yi mamaki ba, dan haka kai tsaye ya ce. “Muna maraba da zuwanka ranka ya daɗe.”       “Uhhm”.    Janar ya faɗa yana yanke kiran.........✍️ Received at 2:38 PMKIƊA A RUWA 2 43 ........Shima Imran lumshe idanu kawai yayi a wajen yana jingina da kujera. Ya san wannan ganawa ba ta siyasa ba ce, ganawa ce ta gaskiya, ta amana, ta zumunci, ta yarda da bashi na tarihi. Ciki ya koma ya sanar ma Faro, dan haka suka nufi ɗakin da Dada yake duk da su a zatonsu har yanzu barci yake.....     ★2:42am★           Shugaban ƙasa Yusuf Shu'aibu Tafida suka iso cikin base ɗin. Fita ce ta sirri dan a cikin ɓadda kama ma yake. Dan haka daga shi sai dogarinsa ne a motar. Su Imran dake faman zaman jiran tsammani na zaune a falo dan tunda suka leƙa ɗakin Dada suka samu yana barci har lokacin basu zauna ba suka sake dawowa falon. Sai dai abinda basu sani ba likimo Dadan yay musu yana jin motsin shigiwarsu a lokacin, baya son su san yasan abinda suke ɓoyewar, dan haka yay likimo ɗin.        Shigiwar Shugaban ƙasa Yusuf Shu’aibu Tafida ba tare da hayaniya ba ya sakasu miƙewa tsaye a tare. Basuyi mamakin ganinsa a shigar ɓadda kamar ba, kuma ba tare da yan rakiya ba sai dogarinsa kaɗai. Sai da ya zauna, dogarin nasa ya juya ya fita a falon sannan yay musu nunin su zauna suma.       Kawuna suka jinjina cikin girmamawa, sannan suka zauna suna gaishe shi. Da kai kawai ya iya amsa musu. Daga haka shiru ya biyo baya na tsawon sakanni kaɗan, babu wanda ya yi magana kowa da abinda ke a ransa.. Janar ne ya katse shirun nasu da faɗin, “Yana ina?”.      Ƙofar ɗakin da Dada yake Faro ya nuna masa. “Ranka ya daɗe yana ciki yana barci”.      “Muje in gansa”. Ya faɗa yana miƙewa. Suma duk miƙewar sukai. Imran a gaba Janar a tsakkiya sai faro ƙarshe. A mamakinsu suna shiga da sallama suka samu Dada a zaune ya jingina da gadon idanunsa a lumshe. Da ɗan sassarfa Imran da Faro suka ƙarasa garesa har suna haɗa baki wajen tambayar, “Ka tashi?”. Idanun sa dake lumshe ya buɗe a hankali ya sauke a kansu. Sai kuma ya jinjina kansa yana maida dubansa kan Janar. Yanda Janar ɗin ke kallonsa ko ƙyaftawa babu ya saka Dada sakin ƙaramin murmushi a karo na farko, sai kuma ya fara ƙoƙarin yaye blanket ɗin da yake ciki cikin nutsuwar sa. Karo na farko shugaban ƙasa ya matso gaban gafon, tsayawa yay a gabansa sosai yana mai dafe hannunsa da girgiza kai alamar kar ya sauka. Nan ma murmurshi ƙarami Dada yayi. Sai kawai Imran ya gyarama janar kujera a gaban gadon suka fice shi da Faro a ɗakin tare da rufe musu ƙofa...        Janar yakai zaune, har lokacin hannunsa na riƙe dana Dada tamkar mai gudun ya ɓace masa, murya ƙasa amma da nauyin fitar sauti ya furta, “Na yi maka laifi. Haysam”.         Dada ya ɗan murmusa, murmurshi irin na dattako da kamewar nutsuwa, sai kwarjininsa ya sake bayyana da cikar kamala. Kaɗan ya motsa lips ɗinsa ya furta, “Ranka ya daɗe, bazaka taɓa zama mai laifi ba a wajena. Duk abinda ka gani a rayuwar bawa ƙaddararsa ce, sai dai idan tazo a mummunar ƙaddarar saɓama UBANGIJI wannan kam daga mu ne da jagorancin shaiɗan. Ina fatan kana cikin ƙoshin lafiya, ina kuma tayaka murnar tare da addu'ar baka ikon sauke nauyi da haƙƙokin al'umma. ALLAH yasa baka cikin shugabannin da zasuyi dana sanin samuwar mulki a garesu a ranar rarrabe ayyuka”.       “Amin ya rabbi Haysam na gode sosai. Sai dai ka sani shi gudanar da wannan mulkin namu ne a tare, dan kana da muhimmanci a cikinsa wajen sauke nauyin haƙƙin al'ummar ƙasar nan. Shiyyasa nake jin kaicon kaina na kasa kare ka da nayi a shekarun baya.”      Dada ya sauke numfashi, kafin cikin nutsuwa irin tasa ya furta, “ALLAH ya fi kowa iko. Shi ne Alƙali mafi adalci. Wannan rubutacciyar ƙaddara ce tun daga alkalamin farko. Sir ka daina damun kanka”        Kai Janar ya jinjina yana sauke numfashi mai nauyi, tabbas ya yarda ilimin addini duniya ne, wanda ya samu wannan ilimin yay kuma aiki da shi ya more, dan kasancewar Haysam a yau ya tabbatar masa da hakan. Sake duban Dada yayi cikin katsewar tunani ya cigaba da faɗin, “Na zo ne ba a matsayin shugaban ƙasa kawai ba. Na zo a matsayin soja… a matsayin mutumin kuma da ke bin ka bashi.”. Ya ɗan dakata, yana kallon idanuwan Dada kai tsaye. “Akwai guba a jikinka Haysam.” Received at 3:59 PM      Dada bai nuna mamaki ba, sai ma murmurshi da ya saki da ɗan taɓe baki kaɗan ya ce, “Na fahimta tun kafin likitoci su faɗa.”      Shugaban ƙasa ya ɗan zuba masa ido da jinjina baiwar da ALLAH yay masa, irin su Haysam wata ajiyar ALLAH ce a cikin al'umma da sai mai hankali ke fahimta, kaɗan ya ɗan murmusa shima cikin baƙin ciki da ɗacin murya ya furta. “Har yanzu kai ne Zak-Shadow ɗin da na sani Haysam. ALLAH ya cigaba da ɗaga darajarka da baka kariya, UBANGIJI ya cigaba da ɗora nasararka akan maƙiyanka?”. Ya ɗan yi shiru na sakan biyu har Dada ya samu damar motsa lips ɗinsa kaɗan wajen amsawa da amin.         “Ba zan iya barinka a nan ba. Za ka tafi waje. A ɓoye. Ba suna, ba matsayi, ba labari kamar yanda muka fara ka ƙarasa jiyyarka a can”.       Dada ya yi shiru na ɗan lokaci, sannan ya furta, “Zan je. Amma ba dan tsirana kawai ba. Sai dai ina kewar Mammah da son ganin su”.      “Na sani Haysam. Amma kayi haƙuri bana son kowa naka ya ganka a cikin wannan halin, in sha ALLAHU wata biyu tamkar gobe ne indai da rayuwa. Mammanka zatafi farin ciki da son ganin Haysam. Saɓanin hakan raunana mata zuciya zaiyi daga ita har ƴan uwanka. Ka duba halin da Imran ke ciki a yanzu haka kawai ya isa misali”.       Cike da gamsuwa Dada ya jinjinama shugaban ƙasa kai. Kafin cikin ɗan furzar da iska ya furta, “Zan dawo in sha ALLAHU. Ba a matsayin wanda aka yima afuwa kawai ba. A matsayin wanda ya dawo ya gyara abin da ya samu karaya daga BURINSA.”       Da ƙarfi Shugaban ƙasa ya sauke ajiyar zuciya yana miƙa masa hannu. Kama hannun nasa Dada yayi sukai musabaha irin ta amintattun sojoji masu kishin ƙasa da tsayayyar zuciya, musabaha ta tarihi, ta alƙawari da cikakkaiyar JARUMTA.       Janar dake murmurshi ya furta, “Ina ji a jikina Haysam, da izinin UBANGIJI a ranar da ka dawo ƙasar nan zata fara canjawa da canji irin na masu son a shinfiɗa gaskiya. Da taku irin na masu girgiza zukatan ɓoyayyun munafukai. Daren gobe in sha ALLAHU zaku wuce”.        “ALLAH ya kaimu”.    Dada ya faɗa...... ================= Ranar Lahadi su Nimrah suka dawo gida da yamma. A kuma ranar Daddy Imran da tunda suka je gidan bai kwana ba dan Ammie ta faɗa musu yana wajen aiki yazo gidan da safe, sun nuna farin cikin ganinsa shima kuma yaji daɗin ganinsu. Dan haka suka zagayeshi da uban surutunsu yana biye musu. A ƙasan ransa kam ji yake badan yau ne tafiyar nan tasu ba daya shiryata da Nimrah a ciki. Amma lokaci ya riga ya ƙure, dan yau ne jirginsu zai tashi ƙarfe goma na dare shi da Haysam. Tunanin ya ture gefe ya cigaba da biye musu, dan sunata masa shagwaɓa wai zasuyi missing ɗinsa saboda ya sanar musu zai yi tafiya, kuma zai jima dan wata ɗaya zai yi ko sama da haka. Da yammar ma da kyar suka yarda suka bi Yaya Khalifa da zai maidasu gida. Shi Daddy Imran yace sai anyi isha'i zai shigo yayi ma Mammah sallama... Da yamma Mu'azz yazo ɗaukar su shima, sai kawai Khalifa yay zamansa dan dama yana da uzirin aikin makaranta. Ammie ta haɗa musu kayan kwalliya da kayan ƙamshi na musamman na turarrukan SHUWA INCENSE AND MORE +234 704 229 3387. Suna da turare wuta da khumra kaloli har uku: black humra, white humra, brown humra. Akwai oil perfume da kullacham da genine da Turare kabasa kaloli uku shima. white, black, and brown. Akwai man kitso, da kayan gyaran jiki masu gyara fata da sanyata laushi da santsi kiyita glowing abinki hajjaju. Duk da kuwa Aunty Biebah ta saya musu kwanaki. Yanzu ɗin ma harda na Biebah Ammie ta bada, sannan taima Mammah gasashen nama mai ɗan karen daɗi itama a kai mata. Suka wuce Asma'u na musu tsiyar yau zatai barci mai daɗi. Lolo kuwa yana islamiyya ma suka wuce da ansha rigima duk da shima fa ya zama ɗan saurayi tunda 2years kawai Rukyn ta bashi. Gasu yanzu suna shekara sha biyar da watanni. Sai da suka fara sauke Fedoo a gidansu, sannan Bintu. Dan gobe in sha ALLAHU Monday ba batun tafiya gidan Mammah a cigaba da shargalle. Su kuma su biyu Mu'azz ya wuce da su gida cike da jin kewar ƴan uwansu da aka rabu. Received at 3:59 P        Maigadi ya buɗe musu gate, Mu'azz ya shige da motar yana samun waje yay parking. Sun fito suna gulmar ƙanin maigadi Sanda dan gayene, akwai son yin gayu sai dai irin namu na ƙauye.       Har zasu wuce ciki sabon driver ya iso wajen yana kiran sunan Nimrah. Kusan lokaci guda Nimrah, Ruky, Mu'azz suka juyo da mamaki. Nimrah da ƙirjinta yay mummunar bugawa da ƙyar ta iya daurewa ta amsa masa. Sai dai ta kasa motsawa taje inda yake sai shine ya ƙaraso. Ledar hannunsa ya miƙa mata yana faɗin, “Yaron nan daya kawo mage ranar ne yace a baki. Yace a gaishe ku ke da yar uwarki”.        Ji Nimrah take kamar jikinta na rawa. Ta dai daure ta amsa tana gyaɗa masa kai dan ta kasa magana. Shi kuma bai damu ba ya juya ya bar wajen. Sai ma Ruky ce dake ƴar dariya cikin tsokana ta ce,.........✍️ Received at 3:59 PMKIƊA A RUWA 2 44 ..........“Da alama fa Sayyadi Kamal ya buɗe wuta Sisi, kwanaki a gidan Aunty Mimi books, kwana biyu da suka wuce ma haka, yau kuma mi muka samu?”.      Har Nimrah ta sakar mata ledar sai kuma ta amshe da sauri saboda tuna takardar cikin wancan saƙon. Dai-dai Mu'azz na ƙarasowa yana tambayar, “Sayyadi Kamal ɗin dai again yau ma?”.        “Ai kuwa dai Yaya Mu'azz, halan bakuyi masa maganar da kuka ce ba?”.    Ruky ta bashi amsa cike da shaƙiyanci. Sai dai kafin yay magana Nimrah tabar gurin da sauri, ga kuma su Yaya Ma'aruff sun shigo suma gidan da alama daga wani waje suke dan a ƙafa suke, sai ya zam hankalinsu Ruky ya rabu har su Yaya Ammar ɗin suka tambayesu lafiya ganin yanda Nimrah ta wuce ciki kamar da sassarfa. Cikin takaici Mu'azz ke sanar musu wai saƙo sayyadinsu na islamiyya ya aikoma Nimrah.        “Saƙon mi?”.     Yaya Ma'aruff ya tambaya. Kallon Ruky Mu'azz yayi da faɗin, “Wlhy Uncle ban sani ba nima. Ruky ce tasan komai duk da dai ranar muna gidan Daddy ya aiko mata books nan ma”.      Hankalinsu duk suka maida akan Rukyn, sai duk taji tsoro ya kamata. Da sauri ta ce, “ALLAH ba komai fa Uncle, kawai dai ina ga litattafai ne.”       Yanda tayi yasa duk suka fahimci akwai abinda ya dace su sani bayan hakan. Dan haka Yaya Ammar ya ce, “Kinga zo nan”.           “Uncle nace fa ba komai ALLAH”.      “Nima ai bance da komai ba Ruky, canai kawai kizo naji.”      Ita tsoronta kar suji son Nimrah yake a musu faɗa, amma babu yanda ta iya ta ƙarasa inda suke. Wani lokacin Yaya Bilal ya fisu sauƙi su ukun nan har Dadan ma. Amma yau sai ga Yaya Ja'afar cikin lallashi yana tambayarta ta faɗa musu bazasu musu faɗa ba. Minene tsakanin Nimrah da Sayyadin nasu?.         “Idan kuma bazaki faɗa ba zan sanar da Yaya.”      Tasan Daddynsu ake nufi, dan haka ta shiga girgiza kai, “A'a Uncle dan ALLAH karka faɗa masa. Dama kawai shi Sayyadin yana son Ninah ne. Amma wlhy bata kulashi, kuma ka tambaya ma kaji”.          “In bata kulashi miyasa yasan gidan ku?”.       Yaya Ma'aruff ne yay magana yanzu. Da sauri Rukyn ta ce, “Randa ya kawo mage ne, sai kuma ranar sunan Baby Nawal ya kai saƙo gidan Mah-mah na books, kuma can gidan ma muka mantasu. Shekaran jiya ma a gidan Daddy haka”         Ammar zai yi magana Yaya Ja'afar ya hanashi ta hanyar riƙe masa hannu, ƙofa ya nunama Rukyn da faɗin, “Shike nan shige ciki”.      Aiko da gudu ta wuce. Koda ta shiga falo ba taga Nimrah ba sai su Aunty Biebah, sai kawai ta rungume Biebah ɗin, kafin ta saketa ta koma kan su Aunty Lailah tana tambayar ina Mammah?. Bedroom suka nuna mata inda Nimrah dama tana ciki, dan itama tana shigowa ta gansu sai ta shanye tashin hankalinta tayi kamar yanda Ruƙayya tayi sannan ta shige bedroom ɗin Mammah. Tana rungume da ita itama Rukyn ta shigo, sai kawai itama ta rungume Mammah ɗin dan kewarta suke ji mai girman gaske...... ==============      Da daddare kamar yanda Daddy Imran ya faɗa yazo yay ma Mammah sallama akan zaije wani aiki. Amma zai jima dan zai iya ɗaukar wata ɗaya ma. Mammah ta jimanta sosai, amma tai masa addu'a ranta duk babu daɗi. Ganin Imran na rage mata kewa Dada sosai a zuciyarta. Shiyyasa bata cika son taga shima zaiyi nesa da su ba. Sai dai babu yanda suka iya tunda aikinsu ne.         Su kansu su Yaya Ma'aruff sunji babu daɗi, dan kamar dai Mammah ɗince Imran na ɗauke musu kewar Dada. Amma da yake su maza ne sai suka danne suka bishi da addu'a suma. Daga nan suka taɓa hira Ruky da Nimrah na jera masa tsarabar da suke so idan zai dawo harda wayoyi. Duk da dai Nimrah dauriya kawai take yi tun ɗazun hankalinta nakan saƙon Sayyidi Kamal da bata samu ta duba ba. Ƙarfe tara dai-dai Imran yabar gidan, daga nan kuma airport zai wuce dan a can zasu haɗu da Dada kawai...       Bayan wucewarsa Nimrah ta faki idonsu ta wuce ɗaki ganin hankalin Ruky ya koma wajen yima su Abees homework ita da Mu'azz. Gabanta sai faɗuwa yake, tana shiga ta maida ƙofar ta rufe harda mirza key dan jikinta ma rawa yake. A haka ta buɗe ledar ta leƙa, a mamakinta yau ma books ne kamar koyau she. Sai dai yau guda ɗaya ne kawai, hisnul muslim ne kuma ƙarami. Received at 4:00 PMJininta na tsinkewa ta ciroshi, haka ta shiga buɗeshi zuciyarta na rawa. Kamar Ranar kuwa sai ga takarda ƙarama a ciki, ɗauka tai ta buɗe.         _Da alama baki duba saƙon ranar ba ko? To ki sani, cigaba da sakacinki na nufin yin dana sani. Duk da kuwa a cikin dana sanin kike shekaru da dama. Idan kuma bakiyi gaggawar dubawa ba zaki dawwama a dana sanin har karshen rayuwarki musamman idan kika fara cin karo da gawar wani a cikin gidank....._     Batama iya ta ƙarasa ba saboda wani yuuuu data risketa na hajijiya. Ta miƙe zambar tana nufar inda suke ajiye handbags ɗinsu. Laluben ta wadda tai amfani da ita a ranar ta shiga yi dan ko books ɗin batama cireba a ciki. Haka ta zazzageta litattafan suka zubo ƙasa. Tsabar ta rikice tama manta littafin da ka rubuta saƙon yake a ciki a ranar, dan haka dukansu ta shiga buɗewa ɗaya bayan ɗaya sai ana ƙarshe taga takardar, ɗauka tai ta sake karantawa, jin book mai jan bango yasa ta ɗaukesa ta fara buɗo shafukan ƙarshe tana duba lamba harta samu wanda akace. Data buɗe shafin bataga komai ba, sai da ta maida zata rufe ta farga da memory card da aka tura ciki sosai kaɗan ake ganinsa. Tana jawo shi ta wani sauke ajiyar zuciya mai nauyi, sai da ta zuba masa ido ranta fal tambayoyin da basu da amsa. Dai-dai nan aka fara buga ƙofa dan haka ta miƙe tana tattare books ɗin da sauri ta maida a bag ɗin, memoryn ta saka a cikin bra dan dole ta nema waya yanzun nan.       Koda taje ta buɗe ƙofar sai taga Afrah ce. Da ƙyar ta daure ta ce, “My Afry ya akayi?”.        “Aunty yunwa nake ji, kuma ke nake so kimin noodles”.      Kai ta iya jinjina mata kawai ta kama hannunta suka fita...... <%><<%>><%>        A yau Adeel ya sake dawowa ƙasar bayan tafiyar kwanaki da yayi amsa kiran mahaifiyarsa. Sai dai masaukinsa na hotel ɗin can ya fara sauka, dan kwana biyu kawai yake ganin zai yi ya sake komawa sai ya kammala uzirin daya taso masa sai ya dawo sannan yayi shirin da yake so. A bazata Hajiya Hasiba da suka samu labarin yaje gida batare da gaya musu ba a bakin First Lady taga kiran nasa a yau. Sai da gabanta ya faɗi, ta daure da ƙyar dai ta ɗaga dan voice call ne na WhatsApp yay mata. Tashi tai a falon dan duk suna zaune ne idan ka cire Mamawo da bata ƙasar ma. Nabeeha na charting da ƙawayenta ne. Su Amima na kallon Film, sai dai hankalin Nabeeha ya rabu ne gida biyu da tunanin hukuncin data gama yanke ma kanta na komawa gidan Abbansu itama kamar Ismat. Dan haka koda taji Momyn tana gaisuwa da yanayin girmamawa taji a ranta Adeel ne, dan duk da tana tare da manyan mutane girman da take bama Adeel da banne dana kowa. Kuma zata iya girme masa, sai dai bazata haifeshi ba a kwatance duk da tayi karatu kafin aure, ita ba'ai mata auren ƙarancin shekaru ba kamar yanda take basu labari........ ((%))★((%))★((%))       Har washe gari duk yanda Nimrah taso samun waya ta saka memoryn nan hakan ya gagara, ba kuma samun wayar ne mai wuya ba, keɓewa gefe ne ta gagara samu. Dan kowa yau na gida su Mammah ce ma ta ɗan fita tare da Uncle Bilal kuma zuwa sha biyu suka dawo. Gashi tana fashin salla. Ruky ce kawai ke shiga yi balle ta fake da wannan. Da dare kuma suna tare da Ruky, bata son fito mata da abinda ke faruwa saboda ance wani zai mutu. Koda Rukyn ta tambayeta ma littafan da Sayyid ya kawo kawai ta nuna mata cewar ta kaisu cikin littatafan su dake shirye a ƴar kanta, wajen yana a ƙasan hannun bene ne matsayin study table ɗinsu.. Ita kuma tana bata labarin yanda sukayi da su Uncle's jiya.        Nimrah bata samu yanda take so ba sai da kowa ya tafi sallar magriba , ta tabbatar sai isha'i kuma. tana ganin Ruky ma ta kabbara salla ta zare jikinta tabar bedroom ɗin zuwa sama da wayar Mammah a hannu, dan tasan itace zata jima bata fargaba fiye da sauran. A sama a kwai ɗakin kusan ƙarshe da ƙofarsa ta ɗan juya ma nasu Yaya Ammar, shi ta shige. Babu kowa a ɗakin babu ma wanda ya taɓa zama cikinsa. Amma akwai kaya da aka ajiye sai dai komai na a leda a jingine kawai.Ƙaramin table ta jawo duk da akwai ƴar ƙura haka ta zauna ta saka wayar Mammah a plane mood dan karma a kira, ta zare memory ɗin ciki ta saka wanda tun jiya ke maƙale a jikinta. Tana tabbatar da ya hau ta wuce wajen videos kawai. Videos uku ne kacal a ciki, jikinka har rawa yake ta shiga na farko tai playing...........✍️        Received at 4:00 PM