"[10/8, 3:42 PM] Binta Lawan: *BEBE'ARTH* 28/8/2020 Wattpad@Rashuna *KATANGA* _Ina matuk'ar godiya ga Allah (S.W.T) da zai ba ni ikon kawo muku wannan littafi mai suna KTG, ina fatan yadda zan fara cikin yalwatacciyar lafiya na kammalashi haka, Amin summa Amin_ _Sak'on gaisuwa ga 'yan uwa da abokan arzik'i, da kuma dukkanin masoyana na kusa da nesa, ina kuma fatan za ku bani had'in kai cikin wannan littafin, kalma d'aya kawai zan gaya muku, alk'alamin ya fi mashi tsini, kuyi k'ok'ari kui nitso ku ninkaya cikin wannan sabon alk'alamin mai suna *KATANGA*_ _Hak'k'in mallaka:_ *RABEE'AH SHU'AYB NABABA* (RASHUNA) ____________ *ONE* _Bismillahir rahamanir rahim._ *SHIMFID'A* Malam Ahmadu an haifeshi a garin Zaria, asalin malantarsa ya gadota ne a gurin mahaifinsa Malam Buba, kasancewar kuma tun ya na yaro mahaifiyarsa ta rasu, tare ya rayu da mahaifinsa har sai da ya yi aure da matarsa Asabe sannan Allah ya karb'i ran malam Buba, daga nan Malam Ahmadu ya ci gaba da jan ragamar mahaifinsa ta malamta. 'Ya'ya uku Allah ya azurtasa da shi, Abdullahi, Maryam sai autansa Shamsu, Abdullahi shine ya gado mahaifinsa amman kuma ba a iya malamtar ya tsaya ba ya na da shago a kasuwa da yake sayar da kayan awo. Malam Ahmadu shine ya zab'awa Abdullahi mata, 'yar amininsa ce k'ud da k'ud da Allah ya karb'i ransu shi da matarsa shekarun baya da suka wuce, kasancewar gidan nasu gidan yawane, kuma auran zumunci akayi tsakanin mahaifan nata, haka take ta watan gari riya a cikin gidan sai uwar bauta da take musu, tausayinta da duba maraicinta da amuntakar da ke tsakaninsa da mahaifinta hakanne yasa ya nemawa Abdullahi auranta, Abdullahi baiyi musu ba kasancewar ya yaba da d'abiunta kuma ta na yawan burgeshi a duk sailin da zasu had'u hakan yasa ya karb'i tayin auranta da hannu bibbiyu. A gurin Asabe wacce yanzu suke kira da Iya aka fara samun k'alubale, inda ta yi tsalle ta dire akan d'anta ba zai auri 'yar makafi ba, kasancewar mahaifanta duk makafi ne, shikuwa Malam Ahmadu yace ta yi kad'an ta hana wannan auran, idan har taga ba'ayi sa ba to tabbas babu ransa a Duniya. Abdullahi da Maimuna sun aminta da juna sosai ya yin da suka fad'a zazzafar soyayya nan da nan magabata suka shiga lamuran nasu, a lokacin ne kuma wanda yake neman auran Maryam me suna Yusuf ya fito, a kano yake a zaune aiki ne ya kawosa zaria, tun ganin farko da yaiwa Maryam ya aminta da ita, bai fara zuwa zance ba sai da Malam ya yi masa izini, daga bisani kuma yace ya turo magabatansa. An tsayar da ranar auran Abdullahi da Maryam lokaci guda . Anan cikin gidan, Malam Ahmadu ya yanki gefe ya yiwa Abdullahi gini, d'akuna uku ne maka² abinsa a wadace, ya yi musu kuma k'ofar gurinsu da ban, sannan kuma ya had'a masa lefe dai-dai da zamanin da suke ciki. Ansha shagalin biki kafin a kawo amarya sashinta, ita kuma Maryam aka kaita unguwar Sabon gari. Lafiya lau zaman Abdullahi da Maimuna yake babu wata matsala ko d'aya, Malam ya d'ebo soyayyar duniya ya d'orawa surukar tasa, kullum in zai shigo gida da abinda zai aika mata da shi, ya yin da Iya kuwa ta bi ta tsaneta, ko kad'an ba ta sakar mata fuska kyara da tsangwama shine tsakaninsu. Wata d'aya da bikinsu Allah ya azurtata da samun juna biyu, tattali da kulawa fiye da wacce take samu ada Malam yake mata, idan ya fita duk abinda ya san me ciki na sha'awa shi yake siyo mata, Iya kuwa tayi ta sababi a tsakar gida ta na masifar ga d'iyarsa can ta na da juna biyun amma ba ya ta tata ya tare a bayan sirika, ya taka k'afa ma yaje ya gano d'akinta baije ba don tsabar tab'ewa da lalacewa, ci kanki kuwa Malam ba yace mata sai dai yai ta murmushi idan ta na yi ya nai mata uzurin k'wak'walwarta ta goce. Cikin Maimuna na shiga wata tara cif, ta haifi kyakkyawar yarinyarta sankace ciya, da hak'oranta guda biyu na k'asa, tsakanin Abdullahi da Malam ban san wanda ya fi wani farin ciki ba, Malam fad'i yake an haifar masa jika 'Yar baiwa, mutane kuwa da wanda Maimuna ta sani da wanda ba ta sani ba sai tururuwar zuwa barka suke, wasu ma don suga hak'oran ne kawai yake kawo su, don duk wanda yazo sai ya d'aga bakin ya gani, sai dai kawai Maimuna ta yi murmushi. Iya kuwa ko lek'owa taga jikarta ba ta yi ba, illa ma bak'in ciki da take kamar ranta zai fita, saboda yadda taga malam ya na rawar k'afa ya samu jika 'Yar baiwa, don har ya siyo raguna biyu tik'a² ya tirkesu bakin nan yak'i rufuwa, Iya kuwa tace. "Inma za ka daina farin ciki ka daina, shawara nake baku ku d'auki 'yar nan ku kaita bakin ruwa don wallahi 'yar aljanu ce ba 'yar baiwa ba. “ Murmushi kawai Malam ya yi baice da ita komai ba don ya san bak'in ciki ne ya taru yai mata yawa. Ansha shagalin suna yadda ba kwa zato, yarinya taci sunan babar Malam AYSHA, Maimuna tace a dinga kiranta da NUSRAT, yayin da Malam ya d'ebo soyayya,tattali gami da kulawa ya aza akan 'Yar baiwa. Wata d'aya tsira Maryam ma ta haifi 'yarta mace taci sunan babar Yusuf RABEE'AH suke kiranta da HIDAYA. Watan Nusrat uku a duniya Iya ta matsawa Ahmadu number sai ya k'ara aure, wata bazawara ce nan mak'otansu da take shigo mata, mijinta mutuwa ya yi kuma mai bala'in kud'i ne, siyayya take yowa Iya sosai da haka ta siyeta, don dama burinta kenan ta tirsasa d'an nata ya aureta, don ta tareshi da buk'atarta ya yi mata kaca² hakanne yasa ta biyo ta gurin Iya. Don a samu zaman lafiya Malam yacewa Abdullahi ya aureta, itama ya bi zab'inta,ko a samu k'iyayyar da takewa Maimuna ta ragu, don fad'i take yaiwa mahaifinsa biyayya amman ita saboda bai d'auketa a bakin komai ba ya watsa mata k'asa a ido ta ya ya kwa za ta k'aunaci Maimuna? Tun sanda aka saka ranar tarewar Bulki Malam da Abdullahi suke kwantarwa da Maimuna hankali ita kuma ta nuna musu hakan ba komai bane dama ai namiji mijin mace hud'u ne. D'aki d'aya shi ya zama na Maimuna, d'aya na Abdullahi d'ayan kuma na Bulki. Ranar juma'a aka d'aura auransu kuma a ranar ta tare, farin ciki gurin Iya ba'a magana kamar ta zuba ruwa a k'asa ta sha, tunda take ba ta tab'a taka gurinsu ba sai a ranar da aka kawo Bulki. To zamansu dai ga shinan da dad'i babu dad'i a haka rayuwar take juyawa. Shekarar Nusrat d'aya Maimuna ta sake haihuwar mace wacce taci sunan mahaifiyar Maimuna SAFIYYA suke kiranta SHUKHURA, wata uku tsira Bulki ma ta haifi 'yarta mace wacce taci sunan Iya na gaskiya ZAINAB suke kiranta da NIMHA, anan fa Iya ta baje kolin gata da soyayya, fad'i take yanzu ne aka haifa mata jika. Tun haihuwar Shukhura sai da Maimuna ta shekara biyar kafin ta haifi wata macen aka saka mata NA'IMA suke kiranta da YUSRA, ita kuwa Bulki ba ta sake haihuwa ba tun daga kan Nimha. Malam yadda kuka san bai da wata jika sai Nusrat, komai ya samu 'Yar baiwa, kayan ciye² kuwa sai ta rage ake samwa k'annenta, ta shak'u da kakan nata fiye da zatonku masu karatu, shima kuma ta shiga ransa sosai da sosai, ya na bata kulawa ne ba wai don fifici ko wani abuba, sai dai shi a ganinsa dole ne jikanka na fari ya banbanta da sauran, saboda gaba d'aya soyayyar da kakewa d'an naka kake 'yebowa ka aza a kansa. Amman a gurin Iya da Bulki cin fuskane kawai, don a nuna ba'a son Nimha, hakan yasa suma suka d'auki dukkanin tsana suka d'ora akan Nusrat. Nusrat Fara ce, amman farinta mai duhu ne, fuskarta siririya ce mai d'auke da siririn dogon hanci, idanuwanta suna da girma matsakaici masu shape d'in k'wan k'walati, cikin idonta fari ne tas ruwa ya kwanta a cikinsa mai maik'o, k'wayar idonta kuwa bak'a ce me silkin brown a ciki, bakinta d'an madai daici ne haka zalika lab'b'anta basu da wani tudu, ko ya ta motsa bakinta wani siririn dimple ne ke bayyana a gefen kumatunta na tsaye wanda yake k'ara fito da zallar kyahunta. Shukhura kuwa fara ce k'al, suna yanayi da Nusrat, amman ta fi Nusrat kyau, kina ganinta kai tsaye za ki kirata kyakkyawa, saboda ita ko ba tai murmushi ba kumatunta a lotse yake, kuma nata irin na kwance ne. Yusra ma fara ce kamar Shukhura, itama ta na yanayi da su, amman kuma ba ta da dimple. A yanzu shekarun Nusrat goma sha biyar a duniya, ta na sss1, su Shukhura kuma shekarunsu goma sha hud'u suna jss 3 auta Yusra kuma shakarunta tara a duniya ta na aji hud'u a primary. Allah ya yiwa Malam rasuwa shekaru hud'u da suka wuce bayan ya yi jinya kad'an, kowa ya ji babu dad'i domin anyi babban rashi mai girma, musamman Nusrat, bayan mutuwarsa ne kuma soyayyar da Abdullahi wanda yanzu suke kira da Baba yakewa Nusrat ta fara bayyana, don har ga Allah ya fi k'aunarta ya na b'oyewa ne saboda kada ya kuma janyo mata bak'in jini. mutum ne me wadatar zuciya, ba wani k'arfi ne da shi ba sai dai rufin asiri na Ubangiji, don sun wuce cin yau da na gobe a gidansa, haka zalika bai bar iyalansa a wulak'ance ba, a ko da yaushe za ka samesu cikin kyakkyawar kamala. Shamsu ya yi aure da matarsa Fiddausi da d'iyarsu Amima sa'ar yusra, sunanta na gaskiya Zainab, shima Iya ya yiwa takwara, a kaduna suke a zaune a saboda anan ne yake aiki, ya ninka yayan nasa sosai a fannin dukiya wanda k'arara Iya ke nuna banbanci tsakaninsu da Baba. Aunty Maryam kuma mijinta ya koma kano da aiki don haka ya d'ebe su suka koma kano da zama, 'ya'yansu hud'u yanzu, Hidaya, Abdul, Hibba, Abbas, suma sosai Iya take ji da su saboda suma mahaifinsu na da kud'i, kuma anai mata aike akan kari. *Wannan kenan* 300 za ku biya domin samunsa cikin sauk'i. 0567838462 NABABA FADILA SHU'AIB GTBANK in kuma katin waya ne ki turo ta wannan layin, shaidarki ta biya ma ki turo cikinta. 09037093702 In katin wayane 400 zaku biya. Garab'asa gareku masoyana, duk wacce ta sayi wannan littafin za ta sami wanda zan rubuta gaba kyauta, ban yadda ki sayi littafina ki dinga turawa gruop ba, in hakan za kiyi ki sameni a layina muyi magana. Allah ka k'arawa mahaifanmu lafiya da nisan kwana. #Team KTG #N.W.A [10/8, 3:42 PM] Binta Lawan: *BEBE'ARTH* Wattpad@Rashuna *KATANGA* ____________ *TWO* Yau ta kama lahadi, duk da suna cikin hutun makarantar boko, su Nusrat duk sun tsefe kawunansu zasu kitso, sai da Nusrat ta fara wanka ta yiwa Yusra ma ta wanke mata kanta ta taje ta shafe mata shi da mai sannan suka shirya zasu tafi, kallon Shukhura Mama ta yi da ta saka hijabi zasu tafi tace. "Ke yanzu ba za ki wankan ba haka za ki bisu?“ Sai da ta fara turo baki gaba kana tace. "To Mama nan da nan d'in sai na yi wanka, abinda yanzun nan za'a mana mu dawo. “ "Allah ya shirya. “ Mama kawai tace ta na mik'awa Nusrat kud'in kitson nasu had'e da fad'in. "Ta fara yi miki kitson, kuma tai miki manya don kinsan yadda yawan kanki yake, kuma ke zan barwa girkin dare don fita zan yi, saura kuma kice a fara yiwa Yusra don na san hali. “ Murmushi Nusrat ta yi, bayan ta saka hannu biyu ta anshi kud'in kana tace. "Mun tafi.“ Maman tace. "Allah ya tsare, ku dai yi addu'a kafin ku fita. “Tace. "Amin, tom insha Allah.“ Tare da jan hannun Yusra suka bi bayan Shukhura da ta fita tun d'azu. Har sun d'an gota gurin Iya ta hango giftawarsu da sauri ta k'walowa Nusrat kira. "Ke ke A'i zo nan. “ Da yake haka take kiranta tun ma Malam na raye, juyowa Nusrat ta yi, Yusra ta turo baki gaba tace. "Wallahi na san aiki za ta sakaki, kawai kizo mui tafiyarmu mu rabu da ita.“ Murmushi Nusrat ta yi tace. "Bara dai naje na ji kiran da take mini.“ "Tak'i ta rabu da ni d'in, shegiya ifrituwa me zunb'utun baki. “ Suka jiyo muryar Iya daga ciki, kuma turo baki Yusra ta yi ta na hararar gurin kafin ta fice waje da sauri, Nusrat kuma ta nufi gurin Iyan ta na murmushi. Gyaran d'aki tace tai mata da wankin band'aki sai 'yan tsunmokaranta ma da tace ta wanke mata. Kallon Shukhura Nana me kitso ta yi tace. "Ina su Yayar taku?“ "Ga sunan suna hanya. “ "To shiga ciki, gani nan bari na k'arasa sharar nan. “ Rufe bakinta kenan Yusra ta yi sallama, kallon ta Shukhura ta yi bayan ta amsa sallamar ta ta tace. "Ina Yayarmun?“ "Ba Iya ce ta kirata ba, har ta na ce mini ifrituwa. “ Wani haushi ne ya kama Shukhura, ta zura takalminta ta fasa shiga d'akin ta fice a fusace Yusra ta biyo bayanta. Kamar an jefota ta shigo ta na kallon Nusrat da ke zubar da shara. "Sannu" Tace mata, kafin ta shige zuwa gurin Iya, iya na ganinta ta d'aure b'arin goron da ta b'antara a gefen zaninta kana tace. "To rasa kunya b'eran tanka, kinzo kimin rashin kunyar taki ne? “ Kar katar da kai Shukhura ta yi tace. "Ashe 'Yar aljanu na da rana tun da har an iya sakata aiki, me yasa ba ki kirawo 'yar lelen taki tai miki ba sai ita za ki saka, amma in abu zaki bayar babu wanda ke gabanki sai Nimha, amman in aikine sai wacce kika raina, don kin san Nimha ko tsintsiya ba za ta iya d'aga miki ba. Bayan kuma kitso zamu je kina gani kuma Mamanmu na zaman jiranmu“ "Tunda dai ba ke na saka ba, ki shige ki bani guri, kiyi can da rashin kunyarki. “ Cewar Iya "Waa aini kin san abinda bazai tab'a yuyuwa bane, don wallahi bazan bautawa wanda bai san ina yi ba, in cin mutumci ne ya taso azo a tarkace mini, lalalala wallahi, itama ita taga za ta iya.“ "Ni kikewa cin mutumci Safiya, Allah ya dawo da Audu, wallahi za ki gane Ubanki na haifa. “ "Amin, ya dawo d'in ki gaya masa, wallahi duka d'aya yamin kinsan sai na bi ta inda zan rama, Allah ya baki sa'a. “ "Wai da sa'ar ki kikeyi ne Shukhura?“ Cewar Nusrat ta na kallonta, ba ta bata amsa ba ta fice ta na zunb'uro baki, Iya kuwa k'ifi² ta yi da ido tunowa da ta yi sanda ta saka Nusrat a gaba ta na zaginta Shukhura ta amshe ta hayayyak'o kamar za ta daketa har sai da Mama ta fito ta kikkifawa Shukhura mari, shine Baba ya na dawowa Iya ta kwashe ta gaya masa, aikwa ranar Shukhura ta sha duka gurin Baba, ita kuwa ta d'auki aniyar wallahi sai ta rama akan Iya, sai da ta bari duhu ya yi ta kad'a karkashinsu me yauk'i taje ta zuba a band'akin Iya,don ta na da tabbacin yanzu za ta fito ta shiga band'akin ta lab'e a bayan k'ofa, Iya na shiga ta yi sufa ta fad'i Shukhura ta fito ta na ta k'yak'yata mata dariya, tace mata kad'an ta gani muddun ta na sakawa Baba na dukanta, Iya kuwa jiki yai tsami da k'yar ta iya mik'ewa. "Yanzu Mama kina kallo ga Iya can ta saka Nusrat aiki.“ Shukhura ta fad'a ta na turo baki gaba. “ "To meye, don ta sakata aiki?“ Mama ta fad'a ta na cigaba da tankad'en da take. "Amma Mama kefa kikace a fara mata kitson saboda za ki bar mata girki.“ "Yanzu kuma na fasa ba, kije ke a fara miki sai ki baro Yusran a can in Yayar taku tazo sa taho tare sai ki karb'i girkin na samu na fita. “ "Amma Mama....“ Dakatar da ita Mama ta yi had'e da fad'in. "Ban san jin komai ki shige kije kiyi abinda na saki. “ Fita ta yi ta na tutturo baki Mama ta girgiza kai had'e da fad'in. "Allah ya shirya. “ Sai da Iya ta kinta tanci dawowar Baba ta fito babban tsakar gida ta k'wama kujera ta na jiran dawowarsa, aikwa ta na jin sallamarsa ta saki kuka me k'arfi, a gigice ya nufota ya na tambayarta. "Lafiya Iya, me ya faru kike kuka haka?" Face hanci Iya ta yi tace. "Wai ni yau A'i za ta kalli tsabar idona ta zageni ta uwa ta uba. “ " 'Yar baiwa.“ Baba ya k'wallawa Nusrat kira, Nusrat da ke d'aki tun da ta dawo daga kitso kanta ke ciwo shine ta nemi guri ta kwanta, ta na jiyo abinda Iya ke cewa Baba gabanta ya yanke ya fad'i, da ta ji kwa ya k'wallo mata kira nan da nan idonta ya yi rau-rau zai fidda ruwa, a hankali ta mik'e ta fito ba tare da ta amsa kiran ba, kallonta Shukhura ta yi da ke kwashe tuwo ta cika k'atuwar kula ta kai d'akinsu, tace. "Kinga dai da abinda ta saka miki ko? kuma wannan ba shi zai hana gobe idan tace yimin kaza kiyi mata ba. “ Ba tace mata komai ba sai juya idonta da tayi da ya fara fitar da ruwa ta nufi tsakar gidan, Shuk'hura kuwa taci gaba da kwashe tuwonta ta na mamakin sanyin hali irin na Nusrat, ta yi k'wafa a hankali, a ranta tace. 'Iya kenan, ai gara ki tab'ani akan ki tab'a Yayarmu wallahi, don ba ki son son da nake mata bane.' Baba na ganin ta taho a sanyaye ya saki murmushi had'e da fad'in. "Taho mana 'yar baiwa. “ Ganin murmushi akan fuskar Baban nata yasa ta samu k'arfin guiwar k'arasawa gareshi, bak'ar ledar hannunsa ya mik'a mata, me d'auke da d'ata manya-manya kasancewar yasan ta na matuk'ar son d'ata, kana yace. "Ga masoyin naki.“ Murmushi me sauti ta saki tace. "Na gode Babana. “ Baki galala Iya ta saki ta na kallonsu daga bisani ta tafa hannuwa tace. "Yau naga lalacewa ni Asabe, yanzu ina gaya maka abinda yarinyar nan ta yi mini amma kai d'ata ka d'auka ka bata, gani ni wacce na yi silar zuwanka duniya ka san da cewa ina mutuwar son ka'za amma baka tab'a siyowa ka bani ni kad'ai a gidan nan ba, sai dai ka siyo gaba d'aya aci, amman ita da yake shafi da mai ce ka ware ta cikin 'yan uwanta uku, ture biyunma tunda su cikinsu d'aya ai ko Nimha ka siyowa don gudun fitina.“ "D'atan da na siyo mata na tabbata ba za ta cishi ita kad'ai ba, rabawa zasui gaba d'aya da ita da 'yan uwanta, zancen kuma Nusrat ta zage ki wallahi Iya ko jikina duk kunne ne bazan tab'a yadda za ta iya zaginki ba, ko da kuwa dukan mutuwa kikai mata a cikin gidan nan, bare kuma na san halinta ba sawa ba fitarwa, da dai Shukhura kika ce to tabbas wannan zan yadda amma 'yar baiwa lalala, sai dai kice Shukhura ce ta zageki kikace 'yar baiwa ce saboda.... ”Da sauri Iya ta dakatar da shi da fad'in. 'Ni wallahi bance maka Safiya ba, ko sunanta ban ambata a gurin nan ba in ba yanzu ba, jama'a ko kunji na ambaci Safiya? “ Ta fad'a da k'arfi yadda 'yan ciki zasu jiyo ta, murmushi Baba kawai ya yi ya ja hannun Nusrat sukai ciki. "Kedai Mero kin haifi jarabar aljanu a gidan nan, yarinya ta bi ta zamar muku masifa duk kunfi k'aunarta cikin 'yan uwanta, su kuma hakan ko kad'an hakan ba ya damunsu, wannan wata iriyar musifa ce? Kai kuwa Audu k'atuwar asara ce ta hau kanka don zan iya dafa qur'ani kafi son wannan 'yar aljanun ko nace 'yar ruwa akan ni da na diroka duniya, bacin haka har maganata za ka k'aryata ka zab'i d'iyarka, babu komai ai gobe Shamsu zai zo garin, Allah sarki d'an albarka na san gobe miyarmu da ka'ji zan cisu har na ture, don ni ina jin idan yazo ma tattara kayana zan na bisa, don wallahi na gaji da cin shinkafa 'yar hausa da tuwon garin masara kullum suna cushe maka a ciki, don na ji ana rad'e rad'en tuwon masara gini yake a cikin mutum, haka kawai na zauna naje na kashe kaina tun wa'adina bai cika ba. “ Sai misalin k'arfe takwas Mama ta dawo, kallon Nusrat da ke kwance ta yi tace. "Ina Mamana, Yusra taci abinci da kika barta tai bacci?” "Cikin gida tace mini za ta shiga tun d'azu, Yusra kuma sai da taci abinci tukunna tai bacci. “ "Lafiyanki kuwa naga kina yatsina fuska? “ Ta tambayeta duk da a ranta mamakin wai Shukhura ce tace ta tafi cikin gida, bayan ba k'aunar zuwa gidan take ba, aike ma da dole take shiga. "To ki tashi ga fura na taho miki da ita kisha sai ki sha magani.“ Da hanzari ta mik'e don dama yunwa take ji kuma har ga Allah ba ta k'aunar cin tuwon donma ta d'an ci d'atan da Baba ya kawo mata duk da wasu sunce shima ya na faifaye ciki, ita kuwa Mama sanin halin d'iyar ta ta yasa ta yo mata guzurin furar. Sauke idanuwanta ta yi akan kular tuwon da Shukhura ta ajiye, a fili tace. "Allah ya shirya mini ke mamana. Maza Nusrat ki gama kije ki kira mini ita. “ Ta na rufe bakinta ta jiyo sallamarta suka amsa mata. "Laa Mamanmu kin dawo ashe? sannunki da dawowa. “ Fuska a had'e tace. "Yauwa, me kika je yi cikin gida? “ "Nifa ba cikin gida nace mata zanje ba, gidan su Farha nace mata za ni kallo.“ Takai k'arshen maganar ta na kallon fuskar Nusrat. "Ban hana ki zuwa kallo ba?to da Babanku kawai zan had'aki na huta, Ke kuma ai ga shinan kin rufa mata asiri ta tonawa kanta. “ Takai k'arshen maganar ta na kallon Nusrat, yayin da ita kuma ta saki murmushi. "Kiyi hak'uri Mamanmu bazan sake ba. “ "Sau nawa kina fad'in haka? “ "Allah da gaske nake Mamanmu daga wannan bazan sake ba. “ "To wancan uban tuwon da kika ajiye da fatan abincinki ne na sati guda ko?“ "Haba² Mama, sai kace wacce uwarta ta tsine mata duniya ta juya mata baya zan jera sati guda ina cin tuwo, tuwonma ba sabo za'a dinga yi mini ba. “ Mama ta so yin dariya amma ta kanne tace. "Koma me zaki ce kice, amma wancen tuwon sai kinyi sati kina cinsa a gidan nan tun da ke kunnenki na k'ashi ne ba ya jin magana, bacin sau nawa zance ki daina cika mini kula kina kawo mini d'aki? “ Sai da ta fara turo bakin nan gaba kana tace. "To kina dai kallo duk ran girkinta sai ta cika kula fam ta kai d'aki, bacin daga ita sai 'yarta d'aya kamar rai, mu kuwa ta milliro mana, ta cikawa Baba da sirikarta kwano, nima kuwa yau na rama na millira musu na millirawa Iya ma, Baba kuwa na cika masa kwano har ya na zuba. “ Salati Mama ta yi ta saki baki ta na kallon Shukhura. "To don ita ta na cika kula ta kai d'aki ita ta shafa, sune mayunwata ba mu ba, ga shinan yanzu kin sakani a bakin duniya, tijarar Iya ma kad'ai ta isheni, don cewa za tai ina sani na baki girkin shiyasa har ga Allah ban son na bar miki girki na fita. “ "A to don wallahi muddun ni nai girki bazan fasa ciko mana kula na kawo d'aki ba, ko ba za muci ba sai dai mui asararsa. “ "Me kika ce?“ Mama ta tambayeta kasancewar k'asa² tai maganar. "A'a cewa na yi kiyi hak'uri bazan kuma ba. “ "To zo ki fice mini da kular, kije ki k'ara musu tuwon.“ Ta na jin haka ta saki k'ara. "Waishhhhhh Mama kashi² ina zuwa ta fice da gudu zuwa ban d'aki, murmushi Mama ta yi a ranta ta na nemawa Shukhura shiriya ta d'auki kular tuwon ta fita, murmushi ma Nusrat keyi tun fara dramar Maman da Shukhura, don dama sun riga da sun saba...... 300 za ku biya domin samunsa cikin sauk'i. 0567838462 NABABA FADILA SHU'AIB GTBANK In kuma katin waya ne ki turo ta wannan layin, shaidarki ta biyama ki turo cikinta. 09037093702. In katin wayane 400 Za ku biya. Garab'asa gareku masoyana duk wacce ta sayi wannan littafin za ta sami wanda zan rubuta gaba kyauta, ban yadda ki sayi littafina ki dinga turawa gruop ba, in hakan za kiyi ki sameni a layina muyi magana. Allah ka k'arawa mahaifanmu lafiya da nisan kwana, Amin. #Team KTG #N.W.A [10/8, 3:42 PM] Binta Lawan: https://chat.whatsapp.com/L7ZWZtJoVg39WGbG36r78I. Pls share *BEBE'ARTH* Wattpad@Rashuna *KATANGA* ____________ *THREE* Ashe ba kallo Shukhura taje ba, can bakin titi taje gurin me saloon ta siyo farata koraye shar da su, ta biya gurin me zob'o ta siyo, ta sayi cewing gum ta jefa a baki sannan ta yo gida, a wani d'an lokon babban tsakar gida ta ajiye faratan da zob'on kana ta shigo. Sai da ta bari d'aya ta gota ta tabbata a lokacin baccin kowa ya yi nisa ta salallab'a a hankula ta zare sakatar gurinsu ta fice, bayan ta d'auko farar hodarsu, ko tsoron duhun dare ba ta yi, bursuna farar hodar ta yi tun daga fuskarta har wuyanta, ta cire hijabinta sai ta bar wata hula me cibiri cibirin gashi a kanta, rigar jikinta dama ta wani tsohon uniform d'inta na islamiya ne da take bacci da ita. Cikin dabara ta man manna faratan a yatsunta da chewing gum, ta d'aga jarkar zob'on nan ta shanye ta bar d'an guntu a ciki, nan da nan bakinta ya yi jajir, ta guntsi ragowar a bakinta, turmi ta taka ta zira hannunta ta saman k'ofar d'akin Iya a hankula ta zare sakatar kana ta tura ta shiga ta mayar ta rufe, kallon Iya da ke bacci akan gado ta yi, sakamakon haska 'yar k'aramar cocilan d'in da ke hannunta da ta yi a ranta tace. 'Za ki gane kurenki ne.' Kan ruwan cikinta ta hau ta zauna, cikin bacci Iya ta ji masifar nauyi ya ziyarceta, a hankula ta bud'e idanuwanta duk a tunaninta madannin dare ne ya danneta, ido biyun da ta yi da Shukhura nan take wani mugun tsoro ya kamata ta bud'e baki za tayi ihu Shukhura ta yi saurin toshe mata baki da wani tsumma da ta yayibo a gefenta, cikin wata iriyar murya me ban tsoro tace. "Kada ki mana ihu a nan, in ba haka ba zamui daga daga da namanki. “ Nan da nan jikin Iya ya fara rawa kar kar ta fara biya duk wata addu'a da tazo bakinta, son tashi take amma gaba d'aya ta k'asa tashi, hannu Shukhura ta Saka ta karto gefen fuskar Iya had'e da juyar da idanuwanta, rintse ido Iya ta yi kafin ta ji saukar muryar Shukhura a kunnuwanta. "Al'quran kika kuma tsangwamar Nusrat a cikin gidan nan sai mun cire miki k'afa d'aya da hannu d'aya, mu kuma maidar miki bakinki k'eyarki, sannan mu d'aukeki zuwa cikin ruwa, kima gode Allah kin fara manyanta da wallahi yau sai mun sakaki murmushi da hak'ori d'aya.“ Iya firgita Iya ta firgita, wani mugun tsoro ne ya kuma shiga jikinta ko k'wak'k'waran motsi ta kasa, ta na san magana amman ba dama saboda ta toshe mata baki da t'summa kuma ta rik'e da d'aya hannunta, um umm kawai take ta na girgiza kai hawaye na zuba a idonta, tausayi ta bawa Shukhura don tasan ta sha nauyi, don Iya irin siraran tsofaffin nan ne, ita kuwa Shukhura ta na da jiki, d'agata ta yi ta sauka daga kan gadon ta cire hannunta daga bakinta had'e da fad'in. "Kada kuma ki sake ki mana ihu don wallahi zan maidar miki da idonki goshi ki zama mai ido d'aya. “ Ta na maganar ne ta na ja da baya, yayin da Iya tace. "Allah ya baku hak'uri wallahi na daina takura mata, ba iya ita kad'ai ba ma wallahi dukansu na daina shiga harkarsu.“ Wani ihu Shukhura ta yi ta na zaro harshe ya yin da Iya ta yi wani hantsile ta koma k'arshen gado goshinta ya bugi da bango, duk azabar da ta ratsa ta k'wak'wal warta amma haka ta d'inke bakinta saboda tsoron kar ta yi ihu a maidar mata da idonta goshi, ja da baya Shukhura ta ci gaba da yi had'e da fad'in. "Kada kuma ki sake ki juyo sai mun b'acewa ganinki in ba haka ba kuma zamui sama da ke zuwa fadar sarkin aljanu. “ Ta na kawowa nan, ta bud'e k'ofa ta fice, ta taka turmi ta maidar mata da sakatar ta, kana ta d'auke turmin ta mayar da shi mazauninsa, sannan ta d'auki hijabinta ta shige ciki, ta na k'ok'arin mayar da sakata ta ji muryar Baba yace. "Waye nan?“ K'irjinta ta ji ya yi wani irin bugu nan da nan wani mugun tsoro ya kama ta ta fara rawa da bakinta. "Um nice, fitsari na fito naga kamar ba'a saka sakata ba, shine na duba. “ Ta na kawowa nan ta yi saurin fad'awa band'aki don gudun kada ma ya fito ya ganta. Fuskarta ta wanke da sabulu, ta cire faratan ta jefa a shadda, kana ta fito ta koma d'aki, sai bayan da ta kwanta a shimfid'arta wata muguwar dariya tazo mata, fashewa ta yi da dariya sosai ta na hango yadda idanuwan Iya suka firfito gaba d'aya kamar na mayyar da aka kama, wata dariyar ta kuma fashewa da ita, Nusrat da ke gefenta ta farka ta na kallonta a tsorace. 'Anya kuwa babu almutsutsai akan Shukhura kuwa. ' Taji zuciyarta ta jefo mata wannan tambayar kafin ta ji muryar Baba ya na k'walo mata kira. " 'Yar baiwa“ "Na'am Baba. “ Ta amsa, ta tashi ta fita jiki a sanyaye. "Lafiya kuwa nake jiyo dariya a d'akin ku?“ "Wallahi Baba Shukhura ce, kuma ban san me takewa dariyar ba, anya Baba ba za'a nema mata magani ba, ni wasu abubuwan in ta na yi gani nake kamar ba ita kad'ai ba. “ Murmushi Baba ya yi yace. "Shukhura. “ "Na'am.“ Ta amsa cikin muryar shagwab'a ta fito ta na sosa kai. "Me ya sakaki dariya cikin tsohon daren nan? “ Sai da ta fara turo baki gaba sannan tace. "Kawai tuno yadda na tumur mushi hadiza d'azu a makarantar allo na yi, tsokanar Yayarmu ta yi ni kuwa na had'a mata jini da majina ta mik'e da k'yar jiki duk yai tsami kamanninta duk sun sauya bakin nan kamar zunb'utun zakara. “ Ta kuma fashewa da wata dariyar. "To jeki ki kwanta, kinga dare ne kada ki kuma dariyar, kinji Mamanmu. “ D'aga masa kai ta yi, ta koma d'aki, ya bita da idanuwa a zuciyarsa ya na nema mata shiriya, duk da a zuciyarsa shima ya fara tunanin ba ita kad'ai bace, don al'amarin nata akwai ban tsoro, shiyasa ya daina dukanta ko me Iya tace tayi mata, don ya san itama Iyan da laifinta, kuma duk irin dukan da zaiwa Shukhuran ba shi zai hana ta samo ta inda za ta rama akan Iya ba. Duban Nusrat ya yi yace. "Je ki kwanta 'Yar baiwa, zamui maganar da Mamanku da safe.“ "Toh“ Tace had'e da juyawa ta koma d'akin, ta na kwanciya Shukhura ta rungumota ta baya ta na sakin dariya. "Ina sonki Yayarmu, matuk'ar ina numfashi bazan tab'a bari a tab'a mini ke ba na k'yale, da a tab'a ki gara ni a tab'a ni. “ Wasu hawaye ne suka zubo a fuskar Nusrat wa'yenda ba ta san dalilin zubowarsu ba, hannu ta saka ta baya ta rik'e hannun Shukhura gam had'e da fad'in. "Nima ina sonki k'anwata, amma don Allah ki daina fad'a kinji k'anwata. “ "Zan daina, idan har aka daina tab'aki, fatana na saka tsoron ki a zuciyar duk me tab'aki, yadda ko ganinki ya yi sai yai shayin yi miki magana." Ta na kawowa nan ta kuma rungumota a haka bacci ya d'auketa saboda ba ta da wuyar yin bacci, Yusra da ta farka ta jita ba jikin Nusrat ba ta yi juyi ta shige jikinta, hannu Nusrat ta saka ta na shafa kanta, ta na shafo kan Shukhura da d'aya hannun, har lokacin hawaye na zuba a idanuwanta, ta tabbata hawayen k'aunar da 'yan uwanta suke mata ne, kyakkyawar Katanga mahaifiyarsu ta gina musu a zuciyoyinsu na k'aunar junansu, babu ruwansu da k'yashi ko bak'in cikin anyiwa wani abu a cikinsu ba'aiwa d'aya ba, ta na fatan soyayya da k'aunar da sukewa junansu suci gaba da ita har k'arshen numfashinsu, kada Allah ya bawa wani nasarar rusa katangar alak'ar da take ginanna a zuk'atansu. Dubanta ta kai ga mahaifiyarsu da ke baccinta cikin kwanciyar hankali, duk abubuwan da suka faru ba ta san anyi ba, kasancewarta me nauyin bacci, shiyasa ko wani abun Baba ke buk'ata a gurinsu sai dai ya k'wallowa Nusrat kira. A b'angaren Iya kuwa k'wak'wame da bango wani wahalallen bacci ya yi gaba da ita, ba tare da ta shirya zuwansa ba. Washe gari da safe Nimha da taje kaiwa Iya abincin kari, kasancewar girkin Ummanta ne, anan ta samu Iya da kumburarran goshi, gefen fuskarta a karce. "Ayya Iya sannu me ya same ki?“ "Ke dai bari 'yar nan, duhun dare ne irin na damuna, na tashi fitsari na nemi cocilan d'ita na rasa nai shahada na fito haka shine na sha k'asa.“ "Ayya sannu Allah ya kiyaye, ga karin kumallon ki nan.“ Cewar Nimha, daga haka kuma ta juya ta fita kafin Iya tace. "Amin. “ Nimha na zuwa ta gayawa Ummanta abinda ya samu Iya, tab'e baki Umman ta yi had'e da fad'in. "Wa ya sani ma ko karkashin aljanar yarinyar cen ta kuma kad'awa ta zuba mata, ni ban tab'a ganin tak'adiriyar yarinya irin Shukhura ba, Iya na cewa Nusrat 'yar aljanu ai Shukhura ce 'yar aljanu ba Nusrat ba.“ Maganar da Umma ta yi kaf a kunnen Shukhura suka sauka, wani murmushi ta yi a ranta tace. 'Allah ya had'amu za kwa kiyi kallon tak'adiranci.' Kowa na gidan sai da ya shiga ya duba Iya, Nusrat da Shukhura a tare suka shiga duba ta, abinda ya bawa Nusrat mamaki ganin Iya ta kirata da Nusrat abinda tsawon rayuwarta ba ta tab'a kiranta da shi ba, sai dai ta kirata da Ai, ba ma za tace Ayshan ba, duk don Malam ya ji haushi. Sannan kuma har suka fito ba ta sanyata aiki ba, kasancewar duk sanda ta shiga gurin ba za ta fito ba sai ta moreta ko ya ya ne, kuma ta na kallon Shukhura ta na ta sunkui da kai ta na matse dariya, shine da suka koma d'aki ta dubi Shukhuran tace. "Wai dariyar me kike ta matsewa ne a d'akin Iya? “ "Yo ba dole na yi dariya ba, kinga kuwa goshinta kamar mulmuleliyar daddawa sai shek'i yake. “ Ta fashe da dariyar da ke cinta tun d'azu. "Allah ban yadda da ke ba Shukhura, duk yadda akai ta dalilinki Iya ta ji ciwon nan. “ " To ni me ta mun da zan saka ta ji ciwo? “ Ta fad'a ta na d'an turo baki gaba. "Kefe kika ce sai kin saka tsorona a zuciyar duk me takura mini, kuma yau kallon da Iya ta yi mini ya bam bamta da wanda ta ke mini a kullum.“ Rik'o hannuwanta Shukhura ta yi had'e da fad'in. "Tabbas 'Yar baiwa ce ke Yayarmu.“ Kana ta shiga labarta mata yadda sukai da Iya ta na dariya, murmushi Nusrat ta yi tace. "Tabbas Iya tai namijin k'ok'ari da ba ta sume miki ba, don in nice wallahi sumewa zan yi, a gaskiya kin d'au hak'k'in 'yar tsohuwa, don ta tsorata sosai tun da gashi ko labarin ainihin abinda ya faru ba ta bayar ba.“ "Wallahi ba wani hak'k'in ta da na d'auka, in hakane ita sau nawa ta na d'aukar hak'k'unanmu. “ Girgiza kai Mama ta yi, a kwance take duk a tunaninsu bacci take, duk abinda Shukhuran ta fad'a ta jishi, kuma ta na nemawa 'yar tata shiriya, don Baba yace da kansa zai dingai mata rubutu ta na sha, don abin nata ya fara yawa duk abinda akai mata tace sai ta rama ko ta halin k'ak'a. "Kya ci gidanku, bari Babanku ya dawo sai na gaya masa, kuma ki tashi kije yau ke za ki mata shara ki wanke mata band'aki. “ Zunb'uro baki gaba tai ta mik'e, don in ba ta ta shi ba ta san Mama na iya jefo mata duk abinda ke kusa da ita, bayan fitarta Mama ta yi tunanin may be taje ta kumai mata wata muguntar don haka ta shiga k'wala mata kira kafin ta tashi ta bi bayanta....... 300 za ku biya domin samunsa cikin sauk'i. 0567838462 In kuma katin wayane ku turo ta wannan layin, shaidarki ta biya ma ki turo cikinta. 09037093702 In katin wayane 400 zaku biya Garab'asa gareku masoyana duk wacce ta sayi wannan littafin za ta sami wanda zan rubuta gaba kyauta, ban yadda ki sayi littafina ki dinga turawa gruop ba, in hakan za kiyi ki sameni a layina muyi magana. Allah ka k'arawa mahaifanmu lafiya da nisan kwana, Amin. #Team KTG #N.W.A [10/8, 3:42 PM] Binta Lawan: *BEBE'ARTH* Wattpad@Rashuna *KATANGA* ____________ *FOUR* Washe gari da safe misalin goma da rabi, zaune suke suna cin jolof in taliya a babban tray, kasancewar Baba ba ya nan ba a gida ya kwana ba kuma girkin Umma ne sai tak'i toya k'osai ta dama zallar kunu kad'ai ta bawa Nimha 200 ta siyo musu iya su da Iya kawai, wannan dalilin ne yasa Mama ta yi musu jolof in taliya saboda kunu kad'ai bazai rik'e cikinsu ba kuma Nusrat ba ta shan kunu sai koko. Muryar Hidaya suka ji ta na k'wallowa Nusrat kira tab'e baki Shukhura ta yi bayan ta zuba taliyar a bakinta tace. "Ga su shafi da mai nan an faso. “ Wata muguwar harara Mama ta jefeta da shi, kawai sai tai murmushi ta sunkui da kai, daga bakin k'ofa Hidaya ta tsaya, ta tsuguna har k'asa ta gaisar da Mama kana ta dubi Nusrat da ke kallonta ta na murmushi, ta yafitota da hannu had'e da fad'in. "Kizo Yaa RJ ne ke kiranki, tsam Nusrat ta mik'e dama jikinta da hijabi saboda ba ta rabo da shi a jikinta ta bi bayan Hidaya suka fice Mama ta bita da idanuwa, Shukhura ce tace. "Nifa Mama sai nake ganin Aunty Maryam kamar ba ta son Yaa RJ ya na kula Yayarmu.“ "Rufe mini baki ko na dakar miki shi da hannuna, na fa gaya miki ba na son irin magan ganun nan ko? Idan ma ba ta son ya kulata naga ta dalilinta duk kuka sanshi.“ "Yi hak'uri Mama, amma kuma in saboda kar wata alak'a ta shiga tsakaninsu ne to ta sha kurumunta in Allah ya yarda mijin Yayarmu ba daga tsatson mijinta zai fito ba ehe. “ Girgiza kai kawai Mama ta yi don zuciya ta kusa ciyota ta k'wala mata mificin da ke kusa da ita, zama Shukhura ta gyara had'e da gyara murya tace. "Mamarmu nidai na gaji wallahi, ko yaushe sai ki dinga hanamu fad'a ana kuma k'wararmu, nidai wallahi idan Baba ya dawo zan kwashe duk abinda matarsa ke mana a gidan nan in gaya masa, haka kawai yanzu da ba dan muna da wannan taliyar ba sai dai fa mu zauna da yunwa har rana da ranar ma ba wani ishashh......“ Dakatawa ta yi da maganar sakamakon mificin da Mama ta rafka mata don taga hararar da take wurga mata ba za ta saka ta rufe mata baki ba sai ta had'a da duka, mik'ewa Shukhura ta yi ta na zunb'uro baki, ta figi hijabinta da ke kan k'ofa, ta na matsar k'wallar k'arya ta fice ta na. "Wallahi na kusa yin maganin wata a cikin gidan nan.“ Ta fad'a da k'arfi yadda Umma da ke d'aki za ta jiyo ta. Aunty Maryam na shiga d'aki ta tarar da Iya da kumburarran goshi. "A'a Iya me ya sameki haka?“ "Zamewa na yi na fad'i na buge da bango. “ "To wannan karcewar ta gefen fuskarki fa?“ "Ke nifa ba na son tambaya, na gaya miki zamewa na yi na fad'i, me kuma kike son ji, kin wani titsiyeni kamar wata uwata sai kinji abinda ya sameni sai kace wani abu za ki iya a kai, mtssss. “ Taja tsaki taci gaba da sababi yayin da Aunty Maryam tace. "Allah ya huci zuciyarki.“ Ta fice daga d'akin, in ba haka ba ba za ta daina sababin ba, ta shiga d'akin Umma don su gaisa. A cikin mota Nusrat ta samu Yaa RJ, tun fitowarta yake sakar mata murmushi ta cikin gilashin motar har ta k'araso gaban motar, a bud'e murfin motar yake don haka ta shiga ciki ta zauna suka had'a ido da Hidaya da ta juya ta koma cikin gidan. Shiru ne ya biyo baya sai kanta da ta sunkuyar k'asa ta na watsa da yatsan hannunta, yayin da shi kuma ya kafeta da idanuwansa, ya na jin wani sabon yanayi a kanta, ya san Nusrat yarinya ce ta yi k'ank'anta ya furta mata kalmar soyayya, amma ya na jin tsoron ya dawo ya tarar wani ya riga shi nasarar karb'ar soyayyarta, sanyin halinta, yanayin tafiyarta, yanayin maganarta komai ya yi dai-dai da yadda yake son matarsa ta kasance. "Ina wuni Yaaya?“ Nusrat ta katse shirun da yake tsakaninsu ta kuma katse shi daga tunanin da ya tafi, rintse idanunwansa ya yi ya busar da wata iska mai sanyi saboda yadda muryarta ta shiga jikinsa ta zauna, wani siririn zoben azurfa ya ciro daga d'an k'aramin yatsan hannunsa. "Muga hannunki. “ Zara zaran yatsunta ta mik'a masa ya zira mata a yatsanta na kusa da babban yatsa. "Daga nan kaduna zan wuce ta nan jirginmu zai tashi zuwa Uk nan da shekara uku zan kammala karatuna na dawo, ki mini alk'awari ba za ki bawa ko wani saurayi damar k'ulla soyayya da ke ba. “ Ba ta gane inda maganarsa ta dosa ba, don haka ta tsira masa idanuwanta kamar me karantar amsoshin tambayoyin da ke dank'are a zuciyarta, yayin da shi kuma yake jin kallon da take masa har tsakiyar zuciyarsa. 'Meye dalilin da yasa ka bani zobe, me yasa zan maka alk'awarin k'in kula ko wani saurayi bayan ba ni da tabbacin sona kake, idan ma sona kake anya auranmu zai yuhu kuwa, kana ganin Aunty Maryam za ta bar Katangar alak'ar da take ginanna a tsakaninsu taci gaba da ginuwa?' Wa'yannan tambayoyin sune cunkushe a ranta amman ta k'asa furta ko da kalma d'aya, ji take bakinta yai mata matuk'ar nauyi. Hannunta ya matsa had'e da fad'in. "Pls Nusrat. “ Tsintar kanta kawai ta yi da d'aga masa kanta, ya saki kyakkyawan murmushi, ya d'auko wata leda ya d'ora a kan cinyarta. "Na gode Nusrat, Allah ya baki ikon cika mini alk'awarina, bari ni zan wuce, ki gaida mini da su Mama. “ "Za su ji insha Allah, Allah ya kaika lafiya, ya kuma baka sa'a akan karatun naka.“ "Aminnnnn“ Yace yana me jin dad'in addu'arta yayin da ita kuma ta fice ba tare da ta d'au ledar da ya ajiye mata ba, murmushi ya yi don ya san za'a rina, a dai-dai lokacin Shukhura ta fito ta na zunb'uro baki, da hannu ya yafitota tazo gareshi, d'an risinawa ta yi ta gaisheshi yace. "Ga leda nan d'auki ki kaiwa Mama kice ina gaisheta.“ "Tom, an gode. “ Ta d'auki ledar shi kuma ya ja motarsa yai gaba. _RIDWAN JIBRIL shine cikakken sunansa yayin da ake masa inkiya da RJ, mahaifinsa da Yusuf mijin Aunty Maryam uwarsu d'aya ubansu d'aya, mahaifinsa ya rasu tun ya na yaro a gurin mahaifiyarsa yake da take aure a kaduna, tun bayan auran Yusuf da Aunty Marya ya d'auko RJ ya dawo gurinsa da zama suka rik'eshi tamkar d'ansu na cikinsu, bayan gama karatunsa na_ _secondary ya turasa Uk acan yake had'a karatunsa a fannin jarida._ _Hidaya da Nusrat tasu tazo d'aya sosai, suna k'aunar junansu hakanne yasa Nusrat take yawan zuwa hutu gidansu, yayin da shak'uwa me k'arfi ta shiga tsakaninta da Rj, har ta rikid'e ta koma soyayya a zuciyar RJ, idan har zaije kaduna gurin mahaifiyarsa sai ya fara tsayawa gurin Nusrat ya yin da k'arara Aunty Maryam ke nuna ba ta son alak'arsa da Nusrat saboda akwai wani buri da suka ci a kansa ita da mai gidanta._ Kwata² Shukhura tak'i yadda ta shiga ko gurinsu, ta na filin babban tsakar gida a zaune ta na dakon zaman jiran Baba ya dawo, don kada ma Mama ta hanata aikata abinda tai niya, ledar da RJ ma ya bata a bakin k'ofar d'aki ta ajiye ta fito don duk kada Mama ta ruguza mata shirinta, ta san dai duk tsiya Baba bazai wuce 12 na rana bai dawo ba saboda ba a gida ya kwana ba. Har kusan k'arfe d'aya Baba bai shigo cikin gidan ba, har ta fara tunanin tashi ta jiyo takun tafiya don haka ta maida idanuwanta kan k'ofar shigowar, aikuwa Baban ne ya yi sallamar ta amsa masa ta nufeshi had'e da d'ora damuwa akan fuskarta, har da fara taro k'walla, gaban Baba ne ya yanke ya fad'i yace. "Lafiya Shukhura me ya faru? “ "Baba.“ "Na'am fad'a mini me ya faru? “ "Dama kullum Mama ce ke hanani gaya maka.“ "Ina jinki.“ "Duk ranar girkin Umma ba ta bamu abinci ishashshe, da kai da Iya da su ta ciccika muku kwano, kuma har d'anye take ragewa ta b'oye, to yau da safe ba ta toya mana k'osai ba zallar kunu kawai ta dama, ta bawa Nimha ta sayo musu su da Iya. “ Ran Babane ya yi mugun b'aci, ya tabbata Shukhura ba za tai masa k'arya ba, shafa kanta ya yi yace. "Jeki ciki zanwa tufkar hanci. “ Cike da murna ta shige ciki ta na jin kamar ta sauke abu me nauyi a zuciyarta ko kad'an ba ta damu da hararar da Mama ke ta zabga mata ba. Sai da ya bari Umma ta gama girki ta raba kowa ta kai masa shima ta kawo masa nasa sannan ya k'wallowa Shukhura kira, ta amsa ta fito da saurinta. "D'auko mini abincinku.“ "Toh." Tace da hanzari ta juya ta d'auko. "Jeki ki anso mini na Iya. “ "Ai yau Iya ba ita kad'ai bace su Aunty Maryam sun zo. “ "Af na sha'afa, da na shiga gurin Iyanma mun gaisa, bar na tan. “ Ya dubi Umma yace "D'auko mun naku, kuma bance ki rage komai ba, inma kin rage da kaina zanzo na duba.“ Tsuru² Umma ta yi da ganinta ka san ba ta gaskiya taje ta d'auko ta kawo masa duban Shukhura ya yi yace. "Je ki d'aki, ki turo mini Mamanku. “ Shukhura na barin gurin Baba ya dubi Umma yace. "Yanzu wannan adalci kenan? Kalli abincin da rai d'aya zai ci, ki dubi na rai biyu duk sun taka wanda rai hud'u zai ci kinwa kanki adalci? Ko iya Nimha kad'ai ai sai ta tashi da wannan abincin, idan ni ba na gani ai Allah ya na ganinki kuma hakk'insu bazai tab'a barinki ba. “ Fad'a sosai Baba ya shiga yiwa Umma kamar zai ari baki, ya shaida mata muddun ta kuma irin rabon nan to sai ta bar masa gidansa, Mama da tazo fad'an ya rufe ta da shi akan me za ta hana a gaya masa irin haka na faruwa a cikin gidansa ya d'au mataki tunda ita ba ta gaya masa ba, ita dai Mama hak'uri ta bashi don sosai Baba ransa ya b'aci, ranar huni ya yi ya na surfawa Umma fad'a, abincinma ya yi zuciya ya k'i ci ya juyewa su Shukhura akan nasu na su Umman ma ya datsi rabi ya k'ara musu akai ya kira Shukhura ta d'auka, Umma kuwa sai huci take kamar ta janyo Shukhura tai ta jibgarta. _____________ Bayan sati guda Baffa Shamsu yazo garin zariya, a lokacin su Aunty Maryam sun koma kwana uku sukai suka tafi. Transfer yake nema zai dawo zariya gaba d'aya hakanne yasa yazo don neman gidan da zasu samu su zauna, duk da nan kusa da gidansu an masa tallansa to dai ya na son siya amman dai ba su gama cininki ba, tun zuwansa Iya tace. "Nidai yau aradu shinkafar gwamnati zanci, don wallahi na gaji da cin shinkafar hausa ina karo da tsakuwa ta na farfasa mini hak'ori, kalli nan kaga yadda duk hak'orina ya farfashe, don haka ma ni wallahi in za ka tafi binka zan, don na gaji da cin tuwon masara kullum da daddare na kwanta, gara a dinga dafa mini taliyar nan ta gwamnati me dad'in gaske.“ Murmushi kawai Baffa Shamsu ya yi yace. "Haba Iya ba na son kina irin wa'yan nan magan ganun kema dai kinsan Yaya yana matuk'ar k'ok'ari, idan yaji abinda kike cewa bazai tab'a jin dad'i ba.“ "To kar ya ji dad'in mana ni ina ruwana, wani k'ok'ari yake banda son 'yarsa da ya fifita a kaina. “ Ko me ta tuna kuma sai tai shiru kana tace. "Mubar ma maganar d'an arzik'i maza je ka siyo mana shinkafar, ka kuma siyo mana kaji don yau mu d'an wasa bakinmu, don rabona da ci nikam ina jin tun kan rasuwar Malam. “ Girgiza kai kawai Baffa Shamsu ya yi ya na mamakin halin mahaifiyar tasu sam ba ta da godiyar Ubangiji, duk zuwan da zaiyi sai sunci kaji a gidan, haka zalika Baba ma idan ya ji aljihunsa da nauyi ya na siyo musu su ci amma wai kunji rabonta da ci tun kan rasuwar Malam. Buhun shinkafa biyu da katan na taliya da macaroni biyu Baffa Shamsu ya siyo musu ya ajiye su a d'akin Mama, ya siyo musu kaji guda biyar manya ² gashi kuma aka taki sa'a girkin Umma ne, don haka Shukhura ta na da 1000 tace bari taje titi ta siyo don ta san 'yar kad'an za'a sanmusu, Nusrat ma na da 1000 sai ta bata ta siyo musu guda biyu kuma manya da su. Ilai kuwa cinya d'aya fukafiki aya sai wuya aya aka saka musu, ko kad'an ba su damu ba Shukhura ta wanke nasu ta tafasa ta fara suya. K'amshin suyar naman Iya ta ji a ranta tace kaddai matar nan ragewa ta yi take soyawa da hanzari ta fito don ta ganewa idonta, ganin Shukhura ce me suyar ta kai hannu za ta d'auka a cikin wa'yanda ta kwashe, Shukhura ta yi saurin d'auke robar hannun Iya ya sauka a k'asa har sai da ya yi k'ara tace. "Auchhhhh“ Don ta ji zafi sosai, Shukhura kuwa ko a jikinta ta murgud'a baki tace. "Ai ba taku bace, wannan tamu ce naje na siyo, da za ki d'auko yamutsats tsan hannunki ki saka mini a ro....“ Ba ta k'arasa ba taji saukar mari a kuncinta, dafe kuncin ta yi ta tsaya ta na kallon Mama da ta fusge robar naman a hannunta ta d'auki cinya manya² guda biyu ta bawa Iyan, sai da Iyan ta ansa kana ta tab'e baki. "Ai da ba ki daketa ba ai na san duk makirci ne irin naki, ke kitsa mata dukkan abinda takeyi a gidan nan, amma ai Shamsu yazo zai mini maganinta. “ Ta na kawowa nan ta fice daga gurin Shukhura ta bita da d'an iskan kallo, Mama ba ta iya cewa komai ba ta koma d'aki Shukhura ta k'wallowa Nusrat kira. "Yayarmu zo ki kama mini na shiga band'aki. “ Nimha tace. "Kawo na miki kan ki dawo. “ "Don aji dad'in d'iba akai d'aki ba, a'a basshi na gode ga Yayarmu nan za ta ansa. “ Umma ta gallawa Nimha harara. "Maganin shishshiginki kenan ga shinan an gab'a miki magana.“ Memakon Shukhura ta shiga band'aki sai ta fice ta yi gurin Iya. "Kina ina yau in kinci naman nan ba Mama ce ta kawoni Duniya ba. “ Iya na jin haka ta yi saurin nad'e shi a leda ta saka a k'ark'ashin gado, dama ajiyeshi ta yi sai ta gama da na cikin miyar. A bakin k'ofa ta cage tace. "Ki fitomun da namana.“ Sai ki d'auka in kin ganshi ai. “ Bin d'akin tai da ido ta na nazarin inda Iyan za ta ajiye naman, ganin kamar idon Shukhuran ya na sauka a k'ark'ashin gado Iya ta yi saurin d'aukewa ta mik'e tsaye. "Sai kizo ki k'wata in baki da kunya. “ Kanta Shukhura ta yi gadan² ta kama hannunta za ta murd'e. "Ke ke ba ki da hankali wai. “ "Eh bani da shi d'in, ta d'auka ta baki naman sannan ki yab'a mata magana kuma kici alqur'an ba ki isa ba. “ Taci gaba da k'ok'arin k'watar naman dai-dai nan Baffa Shamsu ya shigo. Kyakkyawan maruka ya saukewa Shukhura kana ya tambayi ba'asi Iya ta koro masa bayani, hararar Shukhura ya yi da ke tsugune dafe da kuncinta. "Dama ance ba ki da kunya to yau zanyi maganin rashin kunyarki. “ Ya zari cagar radio ya yo kanta ta saki ihu ta yi bayan Iya dai- dai lokacin ya kawo mata duka ya sauka a jikin Iya, Iya ta zunduma ihu tsabar azaba. "Shamsu ka rabu da yarinyar nan dan Allah kar ka daketa, bai saurari Iya ba ya b'anb'aro Shukhura daga jikinta ya hau zuba mata wayar ko ta ina, aikwa ta bud'e murya ta dinga zunduma ihu, Mama ko motsi daga inda take ba tai ba, kuma ta hana su Nusrat zuwa, tace ai gara taji a jikinta gobe ma ba za ta sake ba, Umma kuwa da gudu ta nufo gurin ta na shewa dama a ciki take da ita. Sai da ya yi mata lilis sannan ya k'aleta,ya fice, Iya na gefe ta na ta matsar k'walla don ta san yau kashinta ya bushe gurin Shukhura, yayin da Umma ke ta shewa ta na fad'ar magan ganu. "Yau dai an mana maganin mara kunyar gidan nan, aiyiri yiri yiri yiri. “ Wani kukan kura Shukhura ta yi ta saki wani ihu ta yo kan Umma da gudu, tsoro ne ya kama Umma ta mik'e za ta fice ta yi tuntub'e ta fad'i, yayin da Shukhura ta shiga aljanun k'arya ta dinga cin uban Iya da Umma da sanda dukkanninsu sun jigata sosai, har sai da Mama tazo ta janyeta, suna shiga d'aki ta fashe da dariya a ranta tace. 'Saura Baffa Sham sun.' Mama kuwa zuba mata ido kawai ta yi, don ta d'auki alk'awarin ta daina dukanta daga yau, addu'ar nan ita za ta cigaba da yi mata anai mata rubutu ta na sha. Da jan jiki Umma ta samu ta komo gurinta, ta na jin mugun shakkar Shukhura a ranta, Iya kuwa kuka ta dinga rusawa don yau babu abinda zaisa ta kwana a cikin gidan nan Shamsu yazo su tafi Kaduna ta wuta da wannan jaraba da masifar da Audu ya haifa. Hankalin Shukhura bai kwanta ba har sai da ta sakawa Baffa Shamsu cinnaku biyar manya² a riga ai kuwa ya sha muguwar azabar da ta wuce dukan da yai mata. 300 za ku biya domin samunsa cikin sauk'i. NABABA FADILA SHU'AIB GTBANK In kuma katin wayane ku turo ta wannan layin, shaidarki ta biya ma ki turo cikinta. 09037093702 In katin wayane 400 zaku biya. Garab'asa gareku masoyana duk wacce ta sayi wannan littafin za ta sami wanda zan rubuta gaba kyauta, ban yadda ki sayi littafina ki dinga turawa gruop ba, in hakan za kiyi ki sameni a layina muyi magana. Allah ka k'arawa mahaifanmu lafiya da nisan kwana, Amin. #Team KTG #N.W.A [10/8, 3:42 PM] Binta Lawan: *BEBE'ARTH* Wattpad@Rashuna *KATANGA* ____________ *SIX* Ta b'angaren Alhj Faruoq Fanda kuwa ya na zuwa gida ya sanar da matarsa Hajiya Suwaiba wata yarinya ta yi wuff da zuciyar yaronsu, farin ciki tsanta H.Suwaiba ta shiga had'e da fad'in "Wata yarinya ce wannan mai matuk'ar sa'a Alhaji?“ "Ai ban baro gurin saukar nan ba sai da na saka aka samo mini bayanai a kanta. A nan unguwar cikaji suke zaune, mahaifinta ba wani mai hali bane sai dai rufin asiri na Ubangiji, itace 'ya ta biyu a gurinsa, ta na matakin aji biyu a sss, an shaidu 'yan gidan gaba d'ayansu da tsantsar tarbiya, sunanta na gaskiya Safiyya, amma da Shukhura ake kiranta.“ K'awataccen murmushi H.Suwaiba ta saki tace. "Kai amman na ji dad'i, Allah yasa itace abokiyar arzik'insa, ai banda hidimar saukar nan da muke ta Maryam da ba abinda zai saka ni zuwa naga sirikata a yau.“ Murmushi Alhj ya yi yace. "Don zumud'i irin naki, gobe in sha Allah dai zamu je gaisuwa, da kayan na gani ina so, don har ga Allah na yaba da zab'in yaron nawa, don dama ina gudun ya d'auko mana irin wayayyin yaran nan marasa tarbiya, fatanmu dai Allah yasa ba maganar wani a kanta.“ "Amin., amma ka dai sanar da Hajiya Inna ko, don gara a gaya mata tun wuri za'a yo mata kishiya. “ Ta kai k'arshen maganar ta na dariya, dariyar shima Alhajin ya yi yace. "Ita ai na fara gayowa ta na nan ta cika fam ta na jiran shigowarsa, na san yau dai ba za'a bashi abinci ba nan za'a koro mana shi. “ Alhj Farouq Fanda asalinsa d'an garin Fanda ne, neman kud'i mahaifinsa yazo yi tun Farouq na yaro, a garin kano suka fara zama ya na yin kasuwancinsa kuma Allah yasa masa albarka a ciki, nan da nan ya tara dukiya me d'imbin yawa, Farouq shi kad'ai ne d'ansa wannan dalilin ne yasa ya bashi gata mai yawa, ranar da Faruoq ya gama karatunsa na shari'ah a ranar mahaifinsa ya rasu, sunyi kuka iya kuka da shi da mahaifiyarsa Fatima (Hajiya Inna. ) Bayan rasuwar mahaifinsa ne dukiyoyinsa duk suka dawo k'ark'ashinsa, sannan kuma ya fara aiki a matsayinsa na babban alqali, nan da nan dukiyarsa ta kuma bunk'asa, ga kuma harkokin kasuwancin mahaifinsa hakan ne yasa ya nemi mataimaka kuma ya samu masu aminci, daga kano suka tarkata suka koma zariya da zama a unguwar sabon gari, gida ya dank'ara ba na wasa ba, ya yiwa Hajiya Inna sashinta da ban, zuwansa zariya anan ya had'u da Hajiya Suwaiba suka fara soyayya itama 'yar garin zariyan ce anan unguwar cikaji, ba'a d'au wani lokaci ba akai bikinsa da Suwaiba, Hajiya Inna na mutuk'ar k'aunar sirikar tata, ko kad'an ba ta san wani mugun hali na uwar miji da ake fad'a ba, ta rik'eta tamkar 'yar cikinta, wannan dalilin ne yasa tai alqawarin idan Allah ya azurtata da 'ya'ya maza za ta k'aunaci matansu kamar 'ya'yan cikinta, don a ganinta babu bambamci tsakanin d'anka da sirikar taka tunda an riga an zama d'aya. 'Ya'ya biyu Allah ya azurtasu da su, Mustafa,sai Maryam, sunga gata sosai gurin mahaifan nasu. Mustafa Faruoq Fanda, wanda abokansa ke kiransa da Fanda ya kammala karatunsa na low har ya zama Barrister mai zaman kansa, komai na shi na rayuwa a sashin Hajiya Inna yake don ta na matuk'ar k'aunarsa, Maryam kuwa rayuwarta ta fi k'arfi a gidan kakanninta na uwa acan cikaji, da yake suma da rufin asirinsu, zamanta a cikaji shiyasa islamiyarsu tazo d'aya da su Shukhura, ba ajinsu d'aya ba, da yake aji biyu ne aka had'e akai saukar, itama Maryam ta yi candy ta na jiran sakamako don ta d'ora daga inda ta tsaya. Wannan kenan. Washe gari da safe Iya ta sami Mama a lokacin ta na toya k'osan da zasui kari da shi tace. "Waini Maimuna ba'a kasafta kud'in nan bane? Na ji shiru ba'a ce Iya ga naki ba. “ "Wani kud'i?“ Mama ta tambayeta don ita a tunaninta wasu kud'i ne Baba ya samu da ban. "Ban gane wani kud'i ba, ki jiki da wata iriyar tambaya, to kud'in da jikokina suka samo.“ D'an k'aramin murmushi Mama ta yi tace. "To ki bari in Babansu ya tashi sai ki tambayesa, in kuma in taso miki shi to? “ "Aini na san ba za ki bari a bani ko ficika a kud'in nan ba Maimuna, na rasa me na yi miki a duniyar nan kika bi kika tsaneni daga ke har 'ya'yanki bare ma waccan me tak'adiriyar k'irar samudawa, da fari kamar arnan zabiya, na tabbata da Nimha ce ta samo kud'in nan biyu za'a raba a bani, amman da yake ku mugaye ne an halicci rowa a jininku biyar kun gagara ba ni, kuje kui ta ci insha Allahu sai kun shekara kuna zabga gudawar da ba ta da comlayin, tuban sardauna kawai.“ Shukhura da Nusrat da ke kallo a 'yar k'aramar wayar Mama, duk suna jin abinda Iya ke cewa, zumbur Shukhura ta mik'e ta fito. "Ki gani a kanki me mugun alkaba'i, insha Allahu kanki bakinki zai komo, naga kud'i namu ne ko, to ba za'a bayar d'in ba kiyi abinda za ki, rowa kuwa mu muka yanke mata cibi, kuma zan nuna miki ni babbar tak'adirya ce don naga kwana biyu kin manta da tak'adirancin nawa, inma tuban galadima ne ko wambai tunda mu musulmai ne Alhmdlillh. “ Tun fara maganar Shukhura Baba ya fito, shi yaiwa Mama alamar ta yi shiru daga k'ok'arin dakatar da Shukhura da take har sai da Shukhuran ta kai aya ya ja hannun Iya suka fice da ke neman fisgewa ta na d'an kuka, sai da sukaje d'akinta sannan ya sake ta yai k'asa da muryarsa sosai yace. " Tun da na auro Maimuna gidan nan take d'aukar cin kashinki Iya, ba ta tab'ai miki kallon banza bare musu da ke, amman har ta haihu kina yi a gaban 'ya'yanta wanda Shukhura ba ta iya d'auka har sai ta rama sannan kuma kisa in daketa k'arshe kuma kanki abin zai dawo, amman har yau kink'i daina abubuwan da kike, maganar kud'i kuma da kike yaran nan daga su har mahaifiyarsu biyar basu karb'a ba ni suka barwa saboda hidimar gida da kuma auransu in ya taso amman kuma kinzo kina fad'ar maganganu a kai, yanzu meye ribar sa'insa da jikarki? Dan Allah Iya ki canja, ki dinga jan girmanki.“ Kuka iya ta ja had'e da fad'in. "Tashi ka fita Audu, tashi ka fita nace tun kafin na tsine maka ka bi duniya, har ni za kazo ka gayawa maganganun banza, a gabanka 'yarka tai mini cin mutumci ka kasa d'aukar mataki saboda an baka kud'i? Jeka kawai Audu na barwa Maimuna da 'ya'yanta kai.“ "Kiyi hak'uri Iya, yanzu zanje na lillisa mata jikinta. “ Kukan Inna ne ya tsaya cak tace. "Idan har kana son albarka a gurina kada ka tab'a lafiyar tak'adiriyar yarinyar nan, don wallahi kaf tak'adirancinta za ta sauke mini yau.“ B'oyayyen murmushi Baba ya yi ya tashi ya fita. Yusra da ta dawo daga siyo sikarin da Mama ta aiketa tacewa Mama. "Wasu a mota sunce suna sallama da Baba. “ Baba da shigowarsa kenan maganar ta sauka a kunnensa ya juya had'e da fad'in. "Bari naje naga su waye.“ Sai kuma gashi ya dawo yace Yusra ta d'auko tabarmi, ta d'auko taje ta shimfid'a a soro. Bayan gaishe² Alhj Faruoq ya gabatarwa da Baba abinda ke tafe da su, sannan ya d'ora da cewar. "Da fatan ba maganar wani a kanta. “ Baba yace. "Ba maganar kowa a kanta, kuma na yi masa izini yazo ya nemi soyayyarta idan har ta amince mishi babu abinda zai hana na bashi ita, Allah ya tabbatar mana da alkhairi. “ Godiya Alhj Faruoq sukai da shi da abokinsa da suka zo tare, sannan ya sanya driver d'insa da ya tuk'osa ya fito da akwatin da suka zo da shi, akwati ne mai kyau madai daici, Alhj Farouq yace. "A bawa Shukhura, kayan sun gani suna so ne. “ Baba yace bazai karb'a ba suka ce ai 'yarsu suka kawo, idan kwa bai ansa ba to baiyi na'am da su ba, daga haka sukai masa sallama suka tafi shi kuma ya ja akwatin ya nufi cikin gida...... 300 za ku biya domin samunsa cikin sauk'i. NABABA FADILA SHU'AIB GTBANK In kuma katin wayane ku turo ta wannan layin, shaidarki ta biya ma ki turo cikinta. 09037093702 In katin wayane 400 zaku biya. Garab'asa gareku masoyana duk wacce ta sayi wannan littafin za ta sami wanda zan rubuta gaba kyauta, ban yadda ki sayi littafina ki dinga turawa gruop ba, in hakan za kiyi ki sameni a layina muyi magana. Allah ka k'arawa mahaifanmu lafiya da nisan kwana, Amin. #Team KTG #N.W.A [10/8, 3:42 PM] Binta Lawan: *BEBE'ARTH* Wattpad@Rashuna *KATANGA* ____________ *FIVE* A haka rayuwa take juyawa cikin d'an k'aramin familyn nan, Nusrat ta yi candy, su Shukhura kuma saura shekara d'aya su yi, a lokacin ne kuma aka saka musu ranar saukarsu ta islamiya da yake duk ajinsu d'aya har Nimha. 3/4/2014 shine ya kama ranar saukar tasu. Iya ba ta sauya daga halinta na nuna banbanci tsakanin jikokinta ba har ma ga 'ya'yan nata, don yanzu Baba bai samun cininki sosai a kasuwa sai ya zamto abinci ma Baffa Shamsu ne ke ajiye musu duk wata, saboda ya dawo nan kusa da gidan nasu da zama. Hakan da matarsa ta gani ne yasa ta d'au babban mataki a kansa, abincin da yake sauke musu sai ya koma saukewa gidan su matar tasa duk wata, gaba d'aya ta bi ta mallake shi ta kanainaye shi ba ta bari ya morawa kowa abin biyar face 'yan uwanta, zagi da tsinuwa kuwa ta na shan shi gurin Iya amma a bayan idonta, in a gaban idonta ne kanzil ba ta iya tofawa, saboda abincin da take kawo mata rana da dare kar taje a daina kawo mata ta shiga uku da cin tuwo don yanzu sai su jera sati suna cinsa huni sir, don yanzu rayuwar gidan lallab'ata suke duk abinda Baba ya samo ciki ake k'ok'arin bawa hak'k'insa. 3/4/2014 Ta kama ranar lahadi kenan, ranar da zuk'ata da yawa ke cikin farin cikin kammala saukar karatun alqurani mai girma, za'a bawa kowa allonta na shaidar saukarta, irin wannan ranar ce ko wani bawa ke burin ta riskesa. Tun daga farkon layin makarantar tasu mak'il yake da mutane ko 'yan saukarma ba'a hangowa saboda suna tsakiya a cikin rumfa,banda sautin qira'ar Shukhura mai matuk'ar dad'i babu abinda kake juyowa a gurin mutane da dama sun nutsu suna saurarar karatun da ke saukar da nutsuwa a zuk'ata. Bayan kammala karatun Shukhura ta taso a hankula ta koma gurin zamansu, tun tasowarta FANDA ke binta da kallo, duk da kasancewar ga tsantsar yarinta nan a fuskarta ya na kallo amman kuma ta kama zuciyarsa sosai, tabbas idan ya bari lokaci ya shud'a wani ne zai riga shi mallakarta, don irin su Shukhura ba wanda ake kalla a kau da kai bane, bare nan gaba ta k'ara girma, har ta zauna idonsa ya na kanta, a hankali ya sauke idonsa akan wacce ke Kusa da ita, tabbas ya gano kama a tattare da su ya na kyauta zatan 'yan biyu ne, duk kallon da yake binta da shi mahai finsa Farouq Fanda na lura da shi, ko ma wacce yarinyace wannan tabbas ta taki sa'a gurin d'an nasa, kallo d'aya idan yaiwa mace to tabbas ta taki babbar sa'a, tun kammala karatunsa yake masa zancen aure amma yake tai masa kwana kwane, amman yau yaga alamun d'an nasa yayi kamu, idan kuwa hakane zai fi kowa farin ciki, bare kuma mahaifiyarsa ta ji labari da Hajiya Inna, murmushi ya yi ya na gano yadda Inna za ta d'auki zancen. Kallonsa ya yi har lokacin idonsa na kan Shukhura, wani kyakkyawan murmushi ya saki ya saka bakinsa dai² kunnansa yace. "Da dukkan alamu dai yau yarona yaga matar aure. “ Kunya ce tai mugun kama shi, ashe dai duk abinda yake mahaifinsa na lura da shi, shafa kansa ya yi ya na mai sunkui da kai, shafa kansa Abban nasa ya yi yace. "Soyayya ta na da kyau yarona, Allah yasa matar arzik'i ce. “ A can k'asan mak'oshi ya amsa da "Amin“ Ya na mai jin muguwar soyayyarta a zuciya wannan shi ake kira love at first sight. Bayan kammala saukar aka fara kiran d'aliban da sukai na d'aya zuwa na goma don a basu kyauta. Aysha Abdullahi Ahmad aka fara kira wacce tai na d'aya sannan aka kira Safiyya Abdullahi Ahmad ita tai ta biyu sai Maryam Farouq Fanda da tai na uku daga haka har aka kai na goma duk aka basu Kyaututtukansu, anan Alhaji Faruoq Fanda ya karb'i speaker yai magana akan ya bawa makaranta kyautar million d'aya, sannan ya bawa Aysha Abdullahi Ahmad da Safiyya Abdullahi Ahmad kyautar million d'aya, saboda yaba k'wazonsu, cikin d'alibai kusan 100 su suka d'au matakin na d'aya da na biyu. Nan gurin taro ya hautsine kowa na fad'in albarkacin bakinsa, yayin da wasu ke cewa ai kyautar million biyu gurin Alhaji Farouq Fanda ba komi bace kamar biyar haka yake jin ya cire daga aljihunsa. Iya kuwa sai dashe baki take ta na kuma b'antarar goronta, ta kalli Umma da ranta yai bak'ik'k'irin saboda bak'in cikin Shukhura da Nusrat, harara Iya ta galla mata tace. "An dai yi asarar haihuwa, ace duk kyaututtukan nan da ake rabawa babu sunan Nimha ko d'aya, saboda k'wak'walwarta irin ta jaki ce, amma kalli 'ya'yan albarka, gaskiya Maimuna ta iya haihuwa banda kyaututtukan da suka samo har kyautan million d'aya suka samo mana saboda 'yan arzik'i ne su irin albarka, don ni har ma na fara kasafta nawa kason da za'a bani, na san dai zan samu kamar dubu d'ari biyu, kinga dubu d'ari zan sayi kayan abinci har da su maltina da madara da su k'wai, da taliyar nan me kanannad'ewa ta gwamnati, d'aya dubu d'arin kuma na ajiye a hankula ina zara ina siyo gasashiyar kaza da youghot ina ci da daddare in tayar da kai, wayyo ai a cikin satin nan ma sai an k'asa gane ni zan canja kala saboda cin dad'i, fatar nan tawa da ta fara yamutsewa saboda wahala za ta gyaru, kai Allah dai ya shiwa Maimuna albarka da ta haifo wa'yannan 'yan albarkar, tun da nake ban tab'a rik'e dubu goma ta kaina ba, amman gashi dalilinsu zan rik'e,har dubu d'ari biyi, ni ban san ma tun tuni me ya hanani nuna musu k'auna ba wallahi, amman duk cikin jikokina Allah na gani na fi son su.“ Duk zubar nan da take ita kad'ai take yinta, don Umma ta bar gurin saukar tun sanda ta fara maganar, saboda ganin za ta d'ora mata wani bak'in cikin ne kawai, da ta jujjuya ba taga Umman ba itama sai ta nufo gida ta na tafe ta na kuma kasafta dubu d'ari biyun da za'a bata. Sai kusan k'arfe uku suka baro gurin saukar, saboda an yiyyi hotuna acan, a matuk'ar gajiye dukkaninsu suke, don haka ko waccensu sai da tai wanka kafin su kwanta zuwan jiran yamma ta yi, duk da gidan nasu a cike yake da 'yan hidimar saukar. Da yamma sukai walimarsu anan cikin gidan, kaya iri d'aya suka saka dukansu, Aunty Maryam ce ta d'inka musu, itace ma ta d'au nauyin kayan snacks d'in da suka raba a walimar. Har kusan dare Iya na d'akin Mama tak'i tafiya sai jan Mama take da hira, Mama kwa sai dai tai ta binta da um da umum saboda rashin sabo. "Aini fa ko, tun tuni dama ina sonki da 'ya'yanki dama duk makircin shegiyar matar can ne wallahi, kullum ita kenan kawo mini b'atanci akanku, ai gashinan ta haifi yarinya mai k'wak'walwa irin ta jaki, da k'afafuwanta kamar na babyn roba. “ "Uhm“ Mama tace kawai, ta na mik'ewa don jin ana kiran sallar isha, in ba sallar ta tayar ba Iya ba za ta k'yaleta da wa'yannan zantuttukan nata mara sa kan gado ba, ganin Maman ta tayar da sallah yasa Iya ta tashi ta fice ta na jifan d'akin Umma da banzan kallo, Umma ta na hangota ta labule a ranta tace. 'Makirar mata kawai, insha Allahu k'wandala ba za'a baki cikin kud'in ba inga ta tsiya, ina nan kuma za ki dawo jikina in miki rashin mutumcin da har ki koma ga mahaliccinki baza ki manta shi ba, tsohuwar banza kawai.' Iya tun ta na jiran shigowar Baba yazo a kasafta kud'in, har bacci yai gaba da ita ba tare da ta sani ba, Baba kuwa sai gurin 11 na dare ya shigo, bayan ya rufe gurinsu ya kirawo Mama da su Shukhura anan ya ke gaya musu. "Na kai Accaunt number d'ina makarantarku, Alhmdlillh d'azu na ji kud'inku sun shigo har million d'aya, yanzu me kuke gani za'ai da kud'in?“ Shiru dukkaninsu sukai su na kallon Mama, ganin Maman ba za tai magana ba yasa Nusrat tace. "Nidai Baba a shawarata kawai ka bar kud'in a Accaunt d'inka, in yaso sai a 'yebi wasu daga ciki a siyo kayan abinci, duk wata lalaura da za ta taso sai a magance da kud'in ko kuwa? “ Ta fad'a ta na kallon Shukhura. "Eh Yayarmu, nima hakan nake shirin fad'a kika riga ni. “ Murmushi Mama ta yi, ta na mai yabawa da hankalin yaran nata, kuma taji dad'in abinda suka ce da mahaifin nasu tace. "Na ji dad'i matuk'a da abinda kuka yanke, dama nak'i maganane don na ji ta bakinku, ku tashi maza kuje d'aki, Allah ya yi muku albarka. “ "Amin.“Suka amsa a tare suka tashi suka fita, bayan fitar tasu Mama ta kalli Baba tace. "Ta bakin nasu nima zanyi, ka d'ebi wasu kud'in ka siyo mana kayan abinci, kabar ragowar a asu sun naka, in yaso duk abinda aka d'an samu sai ka dinga ajiye su, saboda kwanan nan za ka ji auran yaran nan ya tashi, kuma duk su ukun nake magana, don Nimha da Shukhura sun fi Yayartasu gab'b'an girma, in suka jero sai ka rantse itace k'aramar su, shiyasa ma ita Yayartasu d'in ba saurayin da ke zuwa gurinta, sab'anin Nimha da Shukhura, bare ma Shukhura babu ranar banza da ba za'a zo ace ana sallama da ita ba, sai na tursasa ta take fita, sai tace ai wai ita Yayarsu ba ta zance. “ "Da gaskiyarki Maimuna, nima ina tunani idan akace mini auran yaran nan ya taso, duk dai da Allah na dogara shi na mik'awa lamurana, tabbas kuma da ace Nusrat na da tsayayye a yanzu zan aurar da ita, tunda ta yi candy tai sauka me kuma za'a jira, amnan tunda babu sai muyi rok'on Allah ya kawo mata na gari, su Shukhura kuwa babu zancen ai yayarsu ba ta zance, shi aure ai lokaci ne ba'a jiran sai yaya tayi sannan k'anwa za tayi, duk wacce ta samu miji zan aurar da ita, fatana dai Allah duk ya had'a su da mazaje na gari, kuma na ji dad'in shawararki hakan kuma za'ai Allah ya shiga lamarinmu ya kuma dafa mana. “ Mama ta amsa masa da. "Amin. “ 300 za ku biya domin samunsa cikin sauk'i. NABABA FADILA SHU'AIB GTBANK In kuma katin wayane ku turo ta wannan layin, shaidarki ta biya ma ki turo cikinta. 09037093702 In katin wayane 400 zaku biya. Garab'asa gareku masoyana duk wacce ta sayi wannan littafin za ta sami wanda zan rubuta gaba kyauta, ban yadda ki sayi littafina ki dinga turawa gruop ba, in hakan za kiyi ki sameni a layina muyi magana. Allah ka k'arawa mahaifanmu lafiya da nisan kwana, Amin. #Team KTG #N.W.A [10/8, 3:42 PM] Binta Lawan: *BEBE'ARTH* Wattpad@Rashuna https://my.w.tt/Cjpv9nxoJ9?utm_ *KATANGA* ____________ *EIGHT* Tun kan ta k'arasa soro k'irjinta ke dukan uku² shikuwa Mustapha alamun tafiyar da ya jiyo ne yasa shi k'urawa k'ofar da za ta fito ido, sai da ta janyo mayafinta ta rufe fuskarta kafin ta tako a hankali zuwa gurin da akai masa shimfid'a da tabarma zuciyarta na harbawa da gudun gaske, can gefe da shi ta samu ta zauna ta sunkui da kanta k'asa kafin tace. "Ina wuni.?“ "Nima ban ganshi ba, tun da dai ba ajiyarsa kika bani ba, idan kwa kina son na amsa miki to ki tabbata kin yaye rufin da ya Katange mini kyakkyawar fuskar da nake da muradin kallo a ko da yaushe. “ K'asa ta kuma yi da kanta ta na murmushi. "Please nidai a taimaka mini, yau kusan sati guda rabon da na ganta, tun a ranar da ta samu babban guri a zuciyata, idanuwana suka aminta da ita, suka tabbatar da itace sanyinsu kuma haskensu.“ "To aini kunya nake ji." Ta fad'a kamar a shagwab'e. "Idan kika sShukhuraki cikin nawa za ki daina jin kunyar. “ 'Cif, na ma kasa bud'e mayafina na ganshi, duk da zuciyata da take ta azalzalata na gansa shine har zan saka idona cikin na, hod'ijam aikam dai sai dai kar na daina jin kunyar' Muryarsa ce ta dawo da ita daga d'an k'aramin guntun maganar zucin da ta tafi. "Zan fa zo da kaina na cire mayafin gaba d'aya wallahi idan har ba ki d'aga sa ba.“ 'Cif saboda kai d'an ikka ne haka kawai ka ciren mayafina, hod'ijam aikam dai da kaga tsigalewa.' K'irjinta ne ya buga, zuciyarta tai wani irin harbawa yayin da ta jisa ya matso dab da ita. 'Laa kaddai ciren mayafin zaiyi kuwa, na shige yau na had'u da mara kunyar mutum.' Da sauri ta yaye mayafin da ke fuskarta, wani kyakkyawan murmushi Mustapha ya saki da yayi sanadiyar motsawar zuciyar Shukhura, wani fitinannen kyahu ta gani a tattare da Mustaphan wanda ba za ta iya bayyana muku shi ba saboda tsabar rud'ewa da cikar kyahunsa. Gira d'aya ya d'age mata had'e da fad'in. "Na miki ne? “ Lumshe idanuwanta ta yi don jin bak'on yanayin da ke sauka a ilahirin jikinta, ta d'au tsayin lokaci a haka yayin da shi kuma yake morewa kallonta son ranshi. Hira suka d'an tab'a kad'an, k'ofofin zuciyar Shukhura sun bud'e gaba d'aya suna d'iban sak'onnin da ke samun babban matsuguni a cikinta, da ya tashi tafiya ya dubeta yace. "A taimaka mini a tura mini hotunan da zasu dinga d'ebe mini kewa. “ Ya fad'a ya na me mik'o mata kyakkyawar wayarsa kamar shi, ta fuskanci yadda yake me kyau haka komai nasa yake me kyau. "Aini bana da hoto ko d'aya.“ "Ko a wayar Yayarmu ne a d'an samo mini mana. “ Don a d'an hirar nan da sukai ta ambaci Yayarmu ya kai wajen sau nawa, anan ya gane da wacce take zaune kusa da ita yai tunanin 'yan biyune itace Yayarmun, kuma ya fuskanci akwai soyayya me matuk'ar girma a tsakaninsu. "Yayarmu ba ta da waya ai. “ "Kawai dai rowa za ki mini, tom shi kenan a gaishe mini da su Mamarmu da Yayarmu da kuma k'annenmu. “ "Tom shikenan zasu ji insha Allah, nima a gaisar mini da so Hajiya, da kuma Hajiya Inna.“ Dariya ya yi had'e da fad'in. "Hajiya Inna za ta ji da kyau. “ Tunowa da ya yi darun da ta saka da Hajiya ta sanar mata su Shukhura ba 'yan biyu bane, Hajiya Inna har da kuka don ita har ga Allah ta saka ran samun tattab'a kunnenta 'yan biyu da zasu dinga sanyata farin ciki, sai da Hajiya ta lallab'a ta tace ai ba dole sai 'yan biyu ne ke haifar 'yan biyu ba, sai kiga ma 'yan biyun basu haifa, ita kuwa idan da rabo sai kiga ta haifa mana, Hajiya Inna tace. "To Allah yasa, amma 'yan biyunne suma suna tafiya da gado, shiyasa na fi samun tabbacin da 'yan biyu ce za ta haifa mana 'yan biyu.“ Zaune suke suna fuskantar juna da wani kyakkyawan bafulatani hannuwanta ya rik'o yace. "Yarinyata hak'ik'a ke haske ce a cikin rayuwar TURAKI ke za ki masa Katanga da damuwar da yake ciki a yanzu, za ki zame masa alkhairi, farin ciki, kuma madubin rayuwarsa. Hak'ik'a Turaki ya na cikin matsananciyar damuwa, kuma ina da tabbacin kece kad'ai za ki iya fiddashi daga ciki, kece za ki d'ora murmushin da ya dad'e da barin kan fuskarsa, ina mai kuma tabbatar miki ke haske ce cikin rayuwarsa domin kece kad'ai za ki yaye duhun da ke lullub'e da shi. “ "To ta ya'ya kake ganin zan zame masa haske bayan ban sanshi ba ban san a ina yake ba, ban kuma san a ina zan same sa ba. “ "Nima ban sani ba, amman kuma ina so ki mini alqawari guda d'aya. “ "Wani alqawari ne ka fad'a ina jinka, zan cika maka shi domin ina maka kallo tamkar mahaifina. “ Shafa kanta ya yi had'e da fad'in. "Na yi matuk'ar farin ciki yarinyata, Allah ya yi miki albarka.“ "Aminnn, ina jinka gaya mini alqawarin.“ "Kada ki bud'e k'ofofin zuciyarki ga kowa bare har ki basu muhalli, har sai lokacin da zai bayyana gare ki sai ki bashi gurbi a ciki ki kuma rufeta gaba d'aya, idan kwa ba haka ba akwai wani abu da zai muku Katanga a tsakani. “ "To amma. “ "Ba na so kice komai, tun da kin riga kin amsa mini tun a farko. “ Shiru tayi, ta na son ta sanar da shine ta riga ta yiwa wani wannan alqawarin, gashi kuma ya katseta, yanzu ya za ta yi, meye mafita gareta? "To meye alak'arka da shi, kuma meye sunansa na gaskiya? “ "Kafin na amsa miki tambayar zan sanar da ke ba za ki sake ganina ba daga yau, kuma ansar wannan tambayar da zan baki itace maganarmu ta k'arshe. D'ana ne shi, amman kuma mutuwa tai mana Katanga a tsakani tun shud'ad'd'an zamani, sunansa na gaskiya ALIYU ana kiransa da Aa............ Girgizata Shukhura ta yi had'e da fad'in. "Yayarmu.“ Wanda hakan ya yi sanadiyar farkawarta daga baccin da take wanda tai mafarkin nan a ciki. "Mtsss kin kama kin tashe ni, gashi ban samu ya fad'a mini sunan da ake kiransa da shi ba yadda in ya bayyana gareni zan ganesa, gashi yace daga yau bazan kuma ganinsa ba. “ Ta fad'a ta na me jin haushin yadda Shukhura ta katse mata mafarkinta ba tare da an gaya mata sunan da ake kiransa da shi ba, to kuma da yake ce masa Turaki waye ke kiransa da hakan? Oho ta bawa kanta ansa. "Kiyi hak'uri, Mama ce tace na taso ki ki k'arasa wanke-wanken yankewa na yi a hannuna in omon ya shiga zafi yake mini kuma bakwan ta kusa da kikace a tashe ki, to amman kuma waye kike kiran ba'a gaya miki sunan da ake kiransa da shi ba? “ "Mafarkin da na gaya miki ina yi ne Shukhura, gashi kuma yace daga yau ba zan sake ganinsa ba, bansan ta inda zamu had'u da Turaki ba Shukhura kuma ban san da wata alama zan ganesa ba. “ "Yayarmu na gaya miki fa ki watsi da lamarin mafarkin nan na ki mafarki fa ba gaskiya ba ne. “ "Wani mafarkin gaskiya ne Shukhura, don na ji ance wasu malaman sunce duk mafarkin da za kayi shi da daddare ka sake yinsa bayan sallar asuba gaskiya ne, wannan dalilin ne nake jin nima nawa gaskiya ne, kuma ina jin hakan a jikina.“ "Wai Shukhura Ina Yayar takun take ne.” "Gani nan Mama. “ Nusrat ta fad'a had'e da ficewa daga d'akin Shukhura ta bita da kallo. Washe gari Mustapha ya dawo ya kawowa su Shukhura ita da Nusrar wayoyi sababbi fil a kwalinsu sai walwali suke da shek'i, murna gurin Shukhura da Nusrat ba'a magana yayin da Umma bak'in ciki kamar ya karta, ta sanya Nimha a d'aki tace. "Kin gani ko, sun fara tura ki a gefe tun kan arzik'in ya ratsasu, yanzu in da da kara ai har da ke za'a kawo wayar. “ " Ni ban ji komai ba Umma, nima Saminu yace k'arshen watan nan zai siya mini. “ "Au yanzu yarinyar nan ba ki sallami Saminun nan ba, yanzu ki rasa wanda za ki mak'alewa sai matsiyacin da babu abinda zai iya tsinana mana.“ Turo baki gaba ta yi ta na had'e rai tace. "Wallahi ni Umma shi nake so ba abin hannunsa ba, idan har zai bani soyayya da farin ciki ya gama mini komai, kuma k'arshen satin nan zai turo magabatansa gurin Baba. “ Ta na kawowa nan ta fice daga d'akin don ta san maganar da za ta fito daga bakin Umman ba mai dad'i bace. "Amman ke dai anyi gantalalliyar yarinya, to wallahi tun wuri kije ki sami Babanku ki sanar masa ba kya sonsa don wallahi muddun rai ba za ki auri matsiyacin yaron nan ba, dudu nawa ne albashinsa da zai iya rik'eki, aike wallahi zubin matan manya ne da ke, amman da yake ba ki san ciwon kanki ba kin lik'ewa wanda babu d'igon arzik'i a tattare da shi, banda haka da kin samo mana wanda zamu shiga cikin dukiya mu kwantar da kai a cikinta a kuma daina mana d'agawa da dukiyar da babu tabbas d'in za'a ji dad'inta.“ A haka rayuwa take tafiya har aka shiga watan azumi, soyayyar Shukhura da Mustapha kuwa ta yi k'arfin da ba kwa zato, har an kawo kud'i an saka rana ta na yin candy, Nimha ma Saminu ya kawo kud'inta tare za'a had'asu da Shukhura, babu haukan da Umma ba ta yi ba, Baba kuwa yace ba ta isa ba, ai arzik'i na Allah ne. Nusrat dai har yanzu babu wanda take saurara har ta kaima yanzu in za ta fita nik'af d'inta take mak'alewa a hammata sai taje soro ta d'aura don kar ma a ganta ace ana sonta, sun sha fad'a sosai da Shukhura har tace sai ta gayawa Mama, sai kuma ta kasa fad'a, ita tausayi ma Nusrat d'in take bata gani take kamar da aljani take yin mafarkin nata da take kira gaskiya. Iya da Nimha kuwa sun dinga mata habaici kenan wai Allah ya yi mata nauyin k'afa gashi har za'a aurar da k'annenta biyu ita ko mashin shini ba ta da, ita kuwa ko kad'an hakan ba ya damunta lokacin auran nata ne bai zo ba idan yazo kowa zai sha mamaki. Mama da Baba kuwa Nusrat d'in tausayi take basu, don Baba har rubutu yake yi ya na bata ta sha na taimako ko Allah zai fito mata da nata mijin itama ya had'asu gaba d'aya ya aurar. Yau aka kai azumi na goma, kuma yaune Mustapha ya kawowa Shukhura kayan Shan ruwa, madara ce peak ta ruwa katan uku sai bomvita babban robar uku milo babban gwangwani uku, sai suger k'aramin buhu, k'wai kiret biyar, sai kuma kayan fruit, Iya kuma ya aiko mata da katan d'in maltina da madara, saboda kullum yazo zance har soro take zuwa su gaisa ya d'an bata hasafi, tun Shukhura na jin takaicin hakan da kunya har tazo ta sake gaba d'aya, don lamarin Iya sai du'ai son abun duniyarta har ya fi na daa. sai tsalle take ta na murna, da yazo da daddare tun kafin Shukhura ta fita ta riga ta fita don ta na ankare da hararar da take zabga mata in taje, har k'asa ta tsuguna ta nai masa godiya kamar za ta ari baki. Umma bak'in cikin duniya ya isheta, ta na kallo aka shige da wa'yannan uban kayan d'akin Mama, ita kuwa Saminu kayan fruit kawai ya kawo sai k'wai kiret uku, takaicin duniya duk ya bi ya isheta ta dinga tsine masa albarka, ji take kamar ta rufe Nimha da duka don ta kaici, amman ta ci alwashin daga bikin Nimhan har na Shukhuran babu wanda muddun rai ba za ta zuba ido 'yarta ta fad'a gidan wahala ba 'yar kishiyarta ta tsunduma gidan hutu ai taci baya, za ta yi duk yadda za tai taga wannan auran bai yi ba, ko na Nimha ya yi to tabbas na Shukhura bazai yuyu ba za ta shiga duk inda za ta shiga ba tare da ta nemi taimakon kowa, saboda daga k'arshe wanda ka nemi taimakonsa shine wanda yake k'ok'arin ganin bayanka, tun da ga shinan a fina finan hausa ana yi da kuma littattafan hausa.......... 300 za ku biya domin samunsa cikin sauk'i. NABABA FADILA SHU'AIB GTBANK In kuma katin wayane ku turo ta wannan layin, shaidarki ta biya ma ki turo cikinta. 09037093702 In katin wayane 400 zaku biya. Garab'asa gareku masoyana duk wacce ta sayi wannan littafin za ta sami wanda zan rubuta gaba kyauta, ban yadda ki sayi littafina ki dinga turawa gruop ba, in hakan za kiyi ki sameni a layina muyi magana. Allah ka k'arawa mahaifanmu lafiya da nisan kwana, Amin. #Team KTG #N.W.A [10/8, 3:42 PM] Binta Lawan: *BEBE'ARTH* Wattpad@Rashuna https://my.w.tt/Cjpv9nxoJ9?utm_ *KATANGA* ____________ *SEVINE* San da Baba ya shiga cikin gidan Umma kad'ai ya tadda da Nimha a tsakar gida suna karyawa, tun shigowarsa Umma ke bin akwatin hannunsa da kallo, ganin ya nufi d'akinsa zai ajiye tace. "Babansu wannan akwatin fa? “ Bai magana ba ya shiga ya ajiye kana ya fito ya k'wallawa Mama kira, ta amsa ta fito. "Kin kai mini ruwan wankan?“ "Eh na kai.“ "To bani kwandon da jallabiyata. “ Duk na kai suna can.“ "To sannu Allah ya yi albarka. “ "Amin.“ Tace ta juya ta koma d'aki, har zai shiga band'aki Umma tace. "Babansu magana fa nake kaimin shiru. “ "Ko ma dai ta meye idan kinyi hak'uri za kiji.“ Daga haka yai shigewarsa band'akin. Sai da yai wanka ya shirya, kana ya karya, sannan ya k'wallowa Nusrat kira, da tazo yace. "D'auki wannan akwatin ki kaimin ita gurin Iya. “ Tace."To“ had'e da d'aukar akwatin ta nufi gurin Iya, shi kuma yacewa su Mama da Umma suzo su same shi gurin Iyan ya biyo bayan Nusrat d'in, Iya na tambayarta wannan akwatin fa dai dai lokacin Baba ya shigo yace. "Ni nace ta kawo, ajiye kiyi tafiyarki. “ Ajiyewa ta yi ta juya ta fita, kafin zuwan su Mama Baba har ya farawa Iya bayani da suka zo kuma ya had'u ya d'ora musu bayanin yadda sukai da su Alhj Faruoq, kafin su bud'e akwatin suga meye a cikinta, lesuka ne 'yan ubansu masu matuk'ar kyau da tsada har kala uku, atamfofi ma uku, sai mayafansu da takalma da jaka, Iya murna da farin ciki kamar ta yi me, sai gud'a take. "Kai Amma wannan yarinya akwai goshin arzik'i, duk inda tai arzik'i binta yake da gudu ya na kamota, gashi har yau mune zamu had'a zuri'a da familyn Fanda, ai abin sam barka ne wannan.“ Umma kuwa bak'in ciki kamar ta yi me kawai yak'en dole take don kar ace ta na bak'in ciki, Mama kam shiru tai ba tace komai ba, Babane yacewa Mama. " ga su nan ki ajiyesu kar tai amfani da su, har sai yaron yazo sun fahimci juna, idan ta aminta da shi to, idan ba ta so ba zan mata dole ba, don haka kece mahaifiyarta ke kika san ta yadda za ki biyo mata. “ "Ai ta aminta da shi ma Audu, wace sakaryar ce za ta k'i zuk'ek'en saurayi d'an gidan Fanda, ga kyau ga kud'i ga ilimi ga kuma ladabi da biyayya, ko ni da nake tshohuwa wallahi ya na mugun birge ni, ai ku kwantar da hankalinku aure kamar anyishi an gama. “ Baba baice komai ba ya yi musu sallama ya tafi kasuwa, sai Umma ce tace. "Iya dama kin sanshi ne? “ "Inma ban sanshi ba tun da ya na son jikata aikwa saninsa ya zama dole. “ Shukhura da Nusrat suka d'ago suka kalli mahaifiyarsu bayan sun gama kallon kayan suka had'a baki gurin fad'in. "Mama kayan waye to?“ "Naki ne Shukhura. “ "Nawa kuma Mama?“ Ta fad'a ta na kallon fuskar Nusrat kafin ta mayar dubanta kan Maman, ita kuma tai musu bayani kamar yadda Baba ya yi mata ta d'ora daa. "Ba dole za'a miki ba Shukhura, ba kuma za'a tab'a musu kaya ba har sai kun fahimci juna kin kuma aminta da shi, sunzo sun nemi izini ne sun kuma kawo kayan na gani ina so. Ki tsayar da zuciyarki guri d'aya, kada dukiyarsu ta rud'e ki ko wani abu na k'yale² idan har bai kwanta miki a rai ba, ki same ni ki gaya mini ni kuma zan gayawa Babanku sai a mayar musu da kayansu a basu hak'uri.“ D'aga kai kawai Shukhura ta yi ta na sunkui da kai k'asa, Mama ta mayar da kallonta ga Nusrat tace. "Yayarsu babu wani wanda ya tab'a tunkararki da zancen soyayya ne?“ Kai tsaye tace. "Eh babu Mama. “ Shukhura ce tai saurin d'ago kai ta kalli Nusrat d'in yayin da Nusrat d'in ta galla mata harara, ganin hakan da Mama ta yi ne yasa tace. "Gaya mini Shukhura waye? In ita kunya ta hana ta fad'a. “ "Babu kowa Mamanmu. “ Shukhura ta bata amsa. "To shikenan tun da ba za ku gaya mini ba, idan Babanku ya dawo kwa gaya masa, Allah dai ya had'aku da mazaje na gari.“ Suka amsa da. "Amin." A tare. Da yamma Hajiya Suwaiba tazo gidan su Shukhura, Mama tai mata tarb'a ta mutumci da girmamawa dai² da k'arfinsu, yayin da Hajiya Suwaiba take ta yabawa da karamcinsu, ta kuma samu sirikartata 💯. Kayan kwalliya ta kawo mata tace ita da 'yar uwarta, don Mustafa yace mata ya na jin fa 'yan biyu ne, Inna kuwa daga jin haka har ta fara murnar za'a haifo musu tagwaye. Tun daga kan mayuka na gyaran fata babu abinda babu a ciki, godiya sosai Mama tai mata, ta rakata gurin Iya suka gaisa, Iya yadda kuka san ta gurfana a gabanta tai mata sujjada aikwa da ta tashi tafiya ta ajiye mata then thauthand, murna gurin Iya ba'a magana ta taho filin tsakar gidansu ta na ta rangad'a gud'a ta na shiwa Mama albarka don ta iya haihuwa tunda ta haifo Shukhura jinin arzik'i. Umma na d'aki takaicin duniya ya bi ya isheta, wani malulun bak'in ciki ne ke damunta, yanzu ta na gani su Maimuna zasu fandama cikin daula, don had'a zuri'a da Familyn Fanda kamar ka tako arzik'i ne, haka za'a mashaheta bora a cikin gidan nan da ita da 'yarta, don Shukhura ba kunya ce da ita, idan ta auri jinin Fanda kanta zai k'ara girma ta kuma taka wanda taga dama, tazo ta na d'agawa k'arshe ma komai na gidan ya dawo hannunta, da ace Nusrat ce ta san ba ta da matsala za ta dubeta tamkar mahaifiyarta, Shukhura kuwa babu abinda take hanga cikin idanuwanta banda tsantsar taya mahaifiyarta kishi, idan kwa ta samu wannan power ta riga ta zama sorry a cikin gidan nan daga ita har 'yarta, don haka dole ne ta nemi mafita tun lokaci bai nemi k'ure mata ba. "Wai meyasa kika cewa Mama ba ki da saurayi? Bayan ga Malam Tajo nan kamar zaiyi hauka a kanki kin kuma k'i ki bashi damar da zaizo ya fallasa asirin zuciyarsa. “ "Bazan tab'a bashi damar hakan ba Shukhura. “ "Saboda me? “ "Saboda girman alk'awari. “ "Hmmm Yayarmu kenan, na tambayeki.“ "Tom Allah yasa na sani.“ "Wai Yaya Rj yace yana sonki ne? “ "A'a baice ba, amman na san ya na dawowa zai gaya mini.“ "Baice ya na sonki ba, amman kike wahalar da kanki gurin zaman jiranshi, baki da tabbas d'in soyayyarki a zuciyarsa, bacin haka Aunty Maryam ba za ta tab'a bari ki auresa ba, domin Hidaya take da burin ya aura. Dan Allah Yayarmu kiyi watsi da lamarin Yaa RJ, ki tsayar da zuciyarki guri guda, kina da samarin nan ki basu dama har ki samu gwani a cikinsu, don ni a ganina Yaa RJ b'ata miki lokaci kawai yake yana kuma wasa da hankalinki, tun da shekara uku yace miki zaiyi ya dawo, yanzu a k'aida saura shekara d'aya kenan amman me Hidaya tace, cewa tai saura shekaru biyu ya dawo, ke a tunaninki Baba zai barki har nan da shekaru biyu a cikin gidan nan, ko kuma za ki cigaba da nuna babu wanda ke zuwa yace ya na sonki? Ta yaya kike tunanin zan karb'i lamarin aurena da muhimmanci bayan ke ba kiyi aure ba, har ga Allah ba na son na yi aure na tafi na barki.“ Hannuwan Shukhura Nusrat ta kama ta rik'e da hannu biyu kana tace. "Ni yanzu ba lamarin Yaa RJ ne ke damuna ba, akwai abinda ke damuna, kuma shi yake hanani karb'ar soyayyar kowa. Kada ki damu da lamarin aurena Shukhura, shi aure lokaci ne, kowa da akwai lokacin da Allah ya rubuta mata, babu ruwansa da wannan yaa ce ko k'anwa duk wacce lokacinta ya yi shikenan, haihuwa, aure da mutuwa duk tafiyarsu d'aya ne suna zuwar maka ne a sanda ba kai zato ba ba kai tsammani ba, don haka kada ma ki sake ki saka a ranki don banyi aure ba kema ba za ki ba, kin san Baba ba zai d'auki hakan ba, kar kuma ki amfani da hakan kice Mustapha bai miki ba, za ki cuci kanki ne don ni ba na hango aurena a nan kusa, ina ji a jikina akwai wasu abubuwa da zasu faru, amman bansan meye su ba.“ "Wani lamari ne ya hana ki karb'ar soyayyar kowa a zuciyarki. “ Wayar Mama ce tai k'ara alamun an kira Nusrat tace. "Kinga har ya k'araso ba ki gama shiryawa ba, maza kiyi² ki k'arasa shirin in kin dawo ma k'arasa maganar, kuma ina fatan k'anin nan nawa ya dagargazo miki zuciyarki kafin ki dawo, kizo kiy tai mini hirarsa ina saurare don naga alamun hakan ma tun a waya. “ Murmushi kawai Shukhura ta yi, don har ga Allah muryar Mustapha ta tafi da ita, sakamakon wayar da suka dunga yi, Maryam k'anwarsa ya turo ta anshi number Mama shine yake kiranta suna gaisawa, burinta kawai ta ganshi a fili don ta na fatan ganinsa ya fi jinsa shikwa ya dinga ja mata aji har sai yau da aka kusa cin sati suna wayar sannan yace mata zai zo. Shi d'inne kuwa yazo, don haka a gaggauce ta k'arasa shiryawa ta fita, Nusrat na ta zolayarta, don sun zamo tamkar wasu k'awaye aminai, don dukansu babu wacce za ta daki k'irji tace ta na da k'awa aminiya sai dai k'awar da za'a gaisa a wuce, sune k'awayen kansu, kuma hakan baisa Shukhura ta raina Nusrat d'in ba........ 300 za ku biya domin samunsa cikin sauk'i. NABABA FADILA SHU'AIB GTBANK In kuma katin wayane ku turo ta wannan layin, shaidarki ta biya ma ki turo cikinta. 09037093702 In katin wayane 400 zaku biya. Garab'asa gareku masoyana duk wacce ta sayi wannan littafin za ta sami wanda zan rubuta gaba kyauta, ban yadda ki sayi littafina ki dinga turawa gruop ba, in hakan za kiyi ki sameni a layina muyi magana. Allah ka k'arawa mahaifanmu lafiya da nisan kwana, Amin. #Team KTG #N.W.A [10/8, 3:42 PM] Binta Lawan: *BEBE'ARTH* Wattpad@Rashuna https://my.w.tt/Cjpv9nxoJ9?utm_ *KATANGA* ____________ *NINE* Shukhura ta rasa yadda za ta yi da Iya, don abin nata kullum k'ara gaba yake, don idan taje su gaisa bai bata ko ficika ba samun guri take ta zauna, ranar da tai mata haka kuwa mantawa ya yi ya fito babu kud'i a jikinsa, ba ta tashi ba har sai da yace. "Iya a mini afuwa ban fito da kud'i ba yau, amma gobe insha Allah za kiga sak'o. “ Takaicin duniya ya ishi Shukhura ji tayi kamar ta nitse a gurin da take a zaune don tsabar kunya yayin da Iya kuwa ta wangale baki tace. "Tom shi kenan jikana babu komi, da yau da gobe duk d'ayane.“ Kunji sai kace ajiya ta bashi, wani d'an iskan kallo Shukhura ta bita da shi a ranta kuwa tace. 'Zanyi maganinki wallahi, yadda ko shi kansa Fandan aka ce gashi a soro ba za ki fito ba, ke ko govnor garinnan El Rufa'i akace gashi yazo zance gurina ba za kiyi gigin fitowa ba.' Fuska taje ta siyo me mugun abun tsoro, sai dagurintaa ruwa bayan an idar da sallar asham, dama lokacin ne dai² zuwansa, tun yamma da tai wanka ta saka riga da wando dama, don haka sai ta d'auko hijabinta har k'asa ta sanya, Mama dama ta na d'akin Baba don haka sai ta cewa Nusrat. "Yayarmu bari na fita soro.“ Tace mata. "Tom. “ Iya na ganin giftawar Shukhura ta fasa tayar da sallar da za tai, don yau ta makara ba ta samu bin jam'in asham ba wani bacci ne ya kwasheta ta na zaune. Murmushi ta yi ta ziro silifas d'inta ta biyo bayan Shukhura ta na k'iyasta yau sallamar da za'ai mata me matuk'ar nauyi ce, don ta na bin bashin wancen zuwan. Shukhura na fita soro ta cire hijabinta ta sak'ala shi jikin k'ofa sannan tai saurin d'aura fuskar ta juya baya. Bakin Iya ya k'asa rufuwa har ta doso soron, dama soron gidan gashi da mugun duhun tsiya, ko hucewa za kai sai ka haska saboda gudun masu lab'ewa, zance ma in zasui sai sun kunna fitila. "A'a yau kuma ba ku kunna fitilar ba ne? “ Cewar Iya ta na tsayawa a dai-dai tsakiyar soron gidan don ba ta hangar komai kar taje ta taka wani daga cikinsu shiyasa tai maganar don su kunna fitila, wani irin dank'a Shukhura taiwa kanta ta had'a fuskokinsu guri d'aya ta sauya magana zuwa me abun tsoro. "Ke wata iriyar nanatacciyar tshowa ce, mu ba ma son mutum me son abun Duniya, daga yau idan Mustapha ya k'ara zuwa kika fito sai mun karya tsila tsilan k'afafuwan nan naki masu kama da Babyn roba, kuma mu shanyar miki da b'arin jikinki gaba d'aya. “ Kar kar kar kawai jikin Iya ke yi uwa mazari ihun da taso ta yi ma ta k'asa wani mugun tsoro ne ya shigeta wanda ba ta tab'a jin irinsa ba. Allahumma inni auzu bika minal kubsi wal kaba isi, kawai take karantawa a ranta kafin Shukhura ta buga mata razananniyar tsawa had'e da fad'in. "B'ace mana da gani tun kafin mu mayar miki da k'afafuwanki a sama kanki a k'asa.“ Fitsari ne zirrrr ya fara bin k'afafuwan Iya kafin ta juya a guje sai ji kake k'um ta bugu da bango ta dawo baya, wata wahalalliyar k'ara ta saki, ta na so ta rarrafa ta bar soron ma ta k'asa anan ta zube a sume tsabar tsoro da rikirkicewa. Umma ce ta jiyo k'arar, don haka ta nufo soro da 'yar fitilarta, ta na haskawa taga Iya a sheme cikin fitsari. "Subhanallahi.“ Shine abinda tace kafin ta juya taje ta kirawo su Baba, ruwa aka watsa mata ta farka a mugun tsorace ganin su Baba kawai ta fashe da mugun kuka, Baba na tambayarta abinda ya faru, kawai cewa take su kamata su kai ta gurinta. Babu yadda Baba baiyi da Iya ba akan ta fad'i abinda ya faru da ita tak'i, k'arshe tace ina ruwansa ya rabu da ita don dole ya k'yaleta Mama ta dubi Nusrat tace. "Kika ce Shukhura na soro, ya kuma ban ganta ba?“ "To nidai Mama haka na ji tace mini, to ina kyauta zaton ban jita dai² ba tun da banga ta d'auki tabarma ba ma.“ Ta na rufe bakinta Shukhura na sallama Nusrat tace. "Yauwa ga ma ta nan.“ Kafin su amsa mata sallamar. "Ina kika je? “ Shine tambayar da Mama ta jefeta da ita, sosa kai tai kafin tace. "Mustapha ne ya kirani gashi a k'ofar gidanmu na fito na anshi sak'o, kuma da na fito ban ganshi ba ina jin zolayata yake, shine muka had'u da 'yar ajinmu muka tsaya muna d'an tattaunawa. “ "Ya yi miki kyau." Mama tace mata, Nusrat kuwa ta kafe ta da idanuwa, ita ta san dalilin kallon da take mata akan abinda ya samu Iya ne ta na zargin Shukhuran ce tai mata wani abu, murmushi kawai Shukhura ta yi, don ta san in ta ritsa ta dole ta gaya mata gaskiya. Tun daga wannan ranar Iya ba ta k'ara gigin fita in Mustapha yazo ba, saboda ita kad'ai ta san azabar da ta sha na jinyar goshinta, shi kuwa da yaga kwana biyu ba ta fitowa shine ya cewa Shukhura zai shiga su gaisa da Iya taje ta gayo mata, ko da Shukhura taje kuwa, iya tace ba ta san zance ba, ta yiwa Allah ta yiwa Annabinsa tace masa yasha zamansa ta yafe duniya da lahira, Shukhura kuwa tace ai kuwa sai ya zo ta fita ta na dariya Iya ta banko k'ofarta ta saka sakata tace sai dai yazo ya gaisar da k'ofa alk'ur'an. Kayan toshi ma da aka kawowa Shukhura k'arara Umma ta nuna bak'in cikinta a gurin, duk da Saminu ma ya yi dai² k'ok'arinsa amman ta raina ta na ta tsine masa albarka, ta na kiransa me kantar talauci, azumi kawai take jira ya k'are ayi sallah ta dugunzuma neman mafita, cikin k'udurar Ubangiji akai sallah lafiya aka gama lafiya, aikuwa ta shiga can cikin k'auyen zariya acan ta samo wani malami, ya shaida mata kud'in aikinta dubu ashirin idan har ta kawo dubu ashirin d'innan to tabbas wannan aure bazai tabbata ba, jiki na rawa ta dawo gida ta sayar da kayan gadonta gaba d'aya ta koma ta kai masa yace to yanzu ta koma taje ta kawo masa k'asar da Mustapha ya taka, idan ta kawota to tabbas da kansa zai zo yace ya fasa wannan aure, shi kuma Saminu za mu juyar masa da ra'ayi da kansa zaice ya fasa auran Nimha, kinga daga nan sai mu juyo da hankalin Mustapha kan Nimha. Farin ciki sosai Umma tai da jin jawabin Malamin, aikuwa ranar da Mustapha yazo ta k'asa ta tsare ta na jiran shigowar Shukhura ta yi sauri ta fice ta d'ebo k'asar da Mustapha zai taka, aikuwa ta na ganin shigowar Shukhuran ta yi saurin ficewa ta 'yebo washe gari taje ta kaiwa malamin aikuwa yace ta na kwance za ta ji kyakkyawan labari... 300 za ku biya domin samunsa cikin sauk'i. NABABA FADILA SHU'AIB GTBANK In kuma katin wayane ku turo ta wannan layin, shaidarki ta biya ma ki turo cikinta. 09037093702 In katin wayane 400 zaku biya. Garab'asa gareku masoyana duk wacce ta sayi wannan littafin za ta sami wanda zan rubuta gaba kyauta, ban yadda ki sayi littafina ki dinga turawa gruop ba, in hakan za kiyi ki sameni a layina muyi magana. Allah ka k'arawa mahaifanmu lafiya da nisan kwana, Amin. #Team KTG #N.W.A [10/8, 3:42 PM] Binta Lawan: *KTG* Wattpad@Rashuna https://my.w.tt/Cjpv9nxoJ9?utm_ ____________ *TEN* KWANCI TASHI Gurin Ubangiji ba wuya, su Shukhura har sun yi candy, sati d'aya da yin candynsu aka kawo lefen su. Akwatina 6 haka Saminu yaiwa Nimha, kuma ya yi iya k'arfinsa kayanta babu kushe ko d'aya, Shukhura kuwa akwatina goma sha biyu dank'are da kaya na alfarma, sark'ok'in daham kuwa zasu kai 6 a ciki, nan da nan hankalin Umma ya k'ara tashi, ta fuskanci wannan malamin kawai kud'inta yake ci dole ta canja shik'a. Wani k'ungurmun boka ta kuma samowa shi ya sanar mata. "Duk wanda yace miki wannan aure bazai tabbata ba to tabbas yai miki k'arya, kud'inki kawai yake ci, wannan aure muk'addari ne daga Ubangiji kuma babu makawa sai ya faru, don haka kije ki rungumi k'addarar da tazo miki da hannu bibbiyu.“ "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, yanzu babu wata mafita? “ " Babu wata mafita indai akan hana auran nan ne, sai dai wani da ban kuma, don wannan ba makawa sai ya tabbata. “ Shiru Umma tai hankalinta in yai dubu ya tashi, yanzu dole ta koma ta d'ebi cin kashi gurin kishiyarta, haka za ta zauna ta na kallon Shukhura na d'agawa da fariya ta na auren me kud'i, komai ta yayibo ta kaiwa uwarta ta na zaune kamar jaka, 'yarta kuwa sai dai ta yayibo kantar talaucinsu ta juye mata, ina bazai yuyu ba da sake, to kuma ta ya ya? Koma ta yaya ne ta bawa zuciyarta amsa daga bisani ta kalli bokon za tai magana ya dakatar da ita da hannu d'aya. "Kud'in aikinki dubu d'ari biyu, za ki kawo mini dubu hamsin da bak'ak'en kaji guda shida, idan aiki ya tabbata sai ki ciko dubu d'ari da hamsin, amman idan har kina so aikin ya kama jikinta sosai sai idan babu ran mahaifiyarta. “ 'Ta yadda da ingancin aikin bokan nan, tun da har ya san abinda ke zuciyarta, to amman kuma ta ya ya mahaifiyarta za ta rasu bayan ranta ba a hannunsu yake ba?.' Maganarsa ce ta dawo da ita daga tunanin da ta tafi. "Zan tura mata ciwon da zaiyi sanadiyar mutuwarta, daga nan ba ki da sauran Katanga tsakaninki da Shukhura, ke za ta dingaiwa kallon mahaifiyarta, amman kafin nan sai an fara raba tsakaninsu da me gidanku, a kuma rufe bakinsa, babu case ga wannan tsohuwar matar idan har kina sakar mata abin Duniya. Su kuma 'yan uwanta za'a raba soyayyar da ke tsakaninsu, saboda ta na matuk'ar son su fiye da son da takewa kanta.“ Farin ciki ne ya dabaibaye zuciyar Umma, ta dinga sharara masa godiya, suka rabu akan za ta dawo ta kawo masa abinda ya Buk'ata.“ Akwatinan Nimha ta kwashe da wasu kaya daga ciki taje ta sayar ta kai masa kud'in da kajin da ya buk'ata, ya bata wani ku'ullikan magani, d'aya ta zuba a cikin abincin da Mama za ta ci, d'aya ta zuba cikin ruwan turaren da za'aiwa Shukhura kamu da shi, d'aya cikin abincin da Baba zai ci, sai laya da za ta saka a bayan gadon Shukhuran, babu wanda zai lura da layar sai ita da ta saka da kanta, sauran abubuwan kuma shi zai ji da komai. Shirye²n biki su Mama suke hankali kwance, don yanzu saura sati guda a fara shagul gulan biki, duk da Mama ta fara fuskantar wasu sauye² daga Baba hakan baisa ta tayar da hankalinta ba, da Allah ta dogara shi kuma taci gaba da mik'awa buk'atunta, don a 'yan kwanakin nan wasu mugayen mafarkai take mara dad'in ji ko kad'an, kawai ta na danne damuwarta ne saboda yaranta, don wani abu da Shukhura kuma ta tsira shine, duk dare sai ta sanyata a gaba ta na kuka ta na rok'onta akan a fasa wannan bikin, ta na jin kamar wani babban al'amari zai tunkaro su idan har akayi wannan auran, sai dai ta lallasheta da nasihohi masu ratsa jiki, don babu damar tunkarar Baba da wannan maganar, bare ya dube su, don ita kanta Mama yanzu ba ta buk'atar auran, to Baban gaba d'aya yanzu ya sauya musu da Nusrat kad'ai yake zama ya yi hira, hakan ya kuma tayar da hankalinsu gaba d'aya amman a haka suka daure suka cigaba da shirye shiryen da ba'a rasa ba. Ranar juma'a akai kamu anan cikin gidan, Iya ce ta kama duka amaren guda biyu, yayin da taiwa Shukhura amfani da turaren Nimha, taiwa Nimha da na Shukhura wannan kuma duk tsarin Umma ne. Ranar juma'ar da daddare akai Dinner d'in gidan su Mustapha, da Baba yace Shukhura ba za ta ba, da k'yar Nusrat ta lallab'a shi ya barsu suka je, kuma diner d'in ta k'ayatar da dukkan wanda ya halarci gurin. Washe gari asabar sukayi walima anan cikin gidan don Baba ya hana DJ kuma walimar ta yi gwanin ban sha'awa. Washe gari lahadi kuma aka d'aura auran. Safiya Abdullahi Ahmad da angonta Mustapha Faruoq Fanda Zainab Abdullahi Ahmad da angon ta. Saminu Yusha'u Hamza. Tun da aka d'aura auran Shukhura da Nusrat ke kuka, gaba d'ayansu suna jin wani miki a zuciyarsu ya na musu ciwo amma ba su san dalili ba, Mama ce tai k'ok'arin rarrashinsu duk da itama ba ta jin dad'in jikinta, amman saboda mutanen da ke shigowa ana kallonsu shiyasa ta rarrashesu, su d'aki falle d'aya bare tace su shiga ciki suyi kukan nasu babu wanda ya gansu, ta san dai kukan rabuwa suke, wannan kuka kuwa dole su yishi, sun taso tamkar 'yan biyun da suka zauna a mahaifa d'aya, suna matuk'ar son junansu ko kyauta za'a yi musu sun fi son ayi musu a tare, idan kwa aka bawa d'aya to tare zasui amfani da shi, musamman Shukhura da ki mata kyauta gara kiyiwa Nusrat za ta fi matuk'ar farin ciki, hakan da Mustapha ya gani ne yasa komai zai yiwa Shukhura sai ya yi musu tare da Nusrat , wataran ma Nusrat d'in kad'ai yakewa kyauta don kawai yaga farin cikin sahibarsa. K'arfe biyar dai² aka kawo motocin d'aukar amarya Shukhura, ita Nimha sai bayan sallar Isha saboda babu nisa, a lokacin kukan Nusrat da Shukhura ya k'ara k'arfi suka rungume juna suna kuka kamar ba sa rabu ba, Iya ce tazo ta janye Shukhura ta na sababi. "Meye kuma na kuka bayan Allah ya 'yanta ki ya kaiki gidan daula, ki daina biyewa Nusrat bak'in ciki take miki don ita Allah ya yota me nauyin k'afar tsiya har yau ko mashin shini babu. “ Shukhura kukanta kawai take, Iya ta dank'ata hannun Aunty Maryam suka shiga da ita d'akin Baba, yayin da Mama ta rungume Nusrat ta na jin itama kamar ta fashe da kukan, takai dubanta ga Yusra da take ta aikin matse k'walla, da hannu ta yafito ta itama tazo gareta ta rungumesu ta na jin wani iri a zuciyarta. Nasihu masu ratsa jiki Baba ya yi mata, ban da kuka babu abinda take ta cikin mayafinta daga k'arshe Baba ya sanya mata albarka aka fito da ita, ganin ana k'ok'arin fita da ita yasa ta fisge hannunta ta ruga d'akinsu da gudu, jikin Mama ta fad'a ta ruk'unk'umeta ta na kuka me ban tausayi, ta na jin kamar shi kenan daga yanzu sun rabu rabuwa ta har abada, shafa kanta Mama ta yi, don ta kusa sanyata zub da k'walla kawai ta na jajircewa ne. "Allah ya yi miki albarka Shukhura, kije kiyi hak'uri ki kuma rik'e gaskiya a duk in da kike. “ "Mama ki yafe mini.“ "Babu abinda kika tab'a yi mini Mamana, ko da kinyi mini nan gaba na yafe miki Shukhura Duniya da lahira, fatana ki rik'e 'yan uwanki da daraja, kada ki bada damar da za'a rusa ginanniyar katangar k'aunar da na gino a tsakaninku tun kuna yara, idan kikai mini haka kin biyani Duniya da lahira, Allah ya yi muku albarka baki d'ayanku, Amin, muje maza ana jiranki. ” Ta rik'o hannunta had'e da na Nusrat, don Yusra tun d'azu ta fice k'ilama har ta samu mota, a hannun Aunty Maryam Mama ta kuma dank'a ta had'e da fad'in. "Allah yasa ki shiga a sa'a, insha Allah mutuwa ce za ta fito dake daga wannan gida cikin salama da aminci, Allah kuma ya baku zaman lafiya na har abada amin, Yayarsu kije ki raka 'yar uwarki d'akinta. “ Daga haka ta saki hannun Nusrat d'in ta shige d'aki, daga jin k'arshen maganarta ka san kuka take. Sai da aka kai Shukhura gurin Hajiya Suwaiba da gurin Inna kana aka huce da ita sashenta dake gefen gidan. Sashen Shukhura gaskiya ya had'u iya had'uwa, komai walwali yake da k'yalli, bed room d'inta ma ciki da falo ne, anan aka yi amfani da kayan da Baba ya siya mata, don cewa sukai ba sai an mata komai ba, Baba yace a barshi dai ya siyawa 'yarsa mutumci, ko ba komai itama za tayi alfahari da haka, kamar yadda ko wace amarya ke yi. Kayan da Baba ya yi musu suma ba laifi sun yi kyau iya kyau. Kowa ya watse daga Shukhura sai Hidaya da suke jiran angwaye su zo suma su kama gabansu, tara dai² Mustapha ya kira Shukhura yace gasu a k'ofar gida zasu shigo don haka sai suka k'ara d'an kimkimtsawa suka fito da ita babban falo suka zauna, abokan nasa biyune sai shi cikon na uku, addu'oi aka yi akan Allah ya basu zaman lafiya kana abokan sukai musu sallama suka fita yabi bayansu don ya yi musu rakiya, su Nusrat ma suka tashi zasu tafi, rik'o hannunta Shukhura ta yi gam tace. "Dan Allah Yayarmu kar ki tafi ki barni.“ Ta fad'a jikinta na rawa, hawaye ne ya zirarowa Shukhura haka zalika Nusrat d'inma suka rungume juna suna kuka, karo na farko kenan da zasu nesanta da juna tun tasowarsu, gurin kwanciyarsu d'aya, filon da suke d'ora kai guda d'aya a haka zasui bacci Shukhura ta rungumo Nusrat ta baya, ta gaba kuma Yusra ta rungumeta, gashi yau zasu kwana ba tare da Shukhuran ba, aure kenan me kawoka wata sabuwar bigiren rayuwa. "Kar ki tafi ki barni, ba na son ki barni, ki zauna tare da ni kinji Yayarmu don Allah.“ "Ai muna tare Shukhura, ba wai mun rabu kenan ba, gobe ma insha Allahu zamu zo, ke dai ki rik'e nasihohin da akai miki, azkhar d'in nan na safe da yamma kada ki sake ki wasa haka zalika nafil fili ma. “ Daga haka ta zare jikinta daga nata ta bi bayan Hidaya saboda tun d'azu Mustapha yace su fito abokansa su sauke su a gida, ledar kaza da youghort Mustapha ya bawa Nusrat ta yi godiya ta shiga motar suka tafi shi kuma ya juya cikin gidan. Ya sha rikici sosai da lallami ya lallamata har sukai sallah suka mika godiyar su ga Ubangiji, daga bisani suka d'an tab'a kazar amarcin don dukkaninsu basu saki jiki sun ci ba, sun d'an jima a zaune, ta na kwance a jikinsa ya kanainayeta kana sukai shirin bacci suka kwanta, Mustapha ya hankad'o ni daga d'akin yace mini. "Asuba ta gari kema kije ki huta. “ Don haka na tafi hutawa sai kuma gobe in kun jini...... 300 za ku biya domin samunsa cikin sauk'i. NABABA FADILA SHU'AIB GTBANK In kuma katin wayane ku turo ta wannan layin, shaidarki ta biya ma ki turo cikinta. 09037093702 In katin wayane 400 zaku biya. Allah ka k'arawa mahaifanmu lafiya da nisan kwana, Amin. #N.W.A #Team KTG #Sonso fisabilillah [10/8, 3:43 PM] Binta Lawan: *KTG* Wattpad@Rashuna https://my.w.tt/Cjpv9nxoJ9?utm_ ____________ *ELEVEN* (ZANEN K'ADDARA) A wannan dare su Nusrat basui bacci ba, zazzab'i ne me zafin gaske ya rufe Mama da kuma matsanancin ciwon kai, wanda bacci ya k'auracewa idanuwanta, haka zalika ma Nusrat ba ta iya rintsawa ba ko kad'an har garin Allah ya waye. Fitowa ta yi ta nufi d'akin Baba don ta sanar da shi sai taji muryar Umma tace. "Nusrat.“ Juyowa ta yi ta na kallonta don ba magana ce ke had'asu ba, face gaisuwa idan Nusrat d'in ta gaisheta. "Cewa na yi Shukhura kuwa ta kiraku? Kinga ni har ta kirawo ta gaisheni." "Ai tun da nai sallar asuba mukai waya da ita. “ Nusrat ta ba ta amsa, don yanzu ba lokacin da za ta tsaya yin tunani akan maganar ba ne, d'akin Baba tai shigewarta, ya na kishin gid'e bacci har zai fara fusgarsa ya ji alamun shigowar mutum, a hankula ya sauke idanuwansa akan fuskar Nusrat yace. " 'Yar baiwa lafiya? “ "Baba, Mama ce ba ta da lafiya tun cikin dare. “ "To sai akai ya ya kuma. “ Tsura masa ido Nusrat tai, kamar ba Baban nan nasu ba, mai k'aunar mahaifiyarsu, ta hango lokacin da tai wata rashin lafiya yadda duk ya firgice ya fita daga hayyacinsa, ya zamo tamkar shine mara lafiyar. Wani yahu me tauri ta had'iye tace. "Dama chamise zamu je. “ "To sai kun dawo don ni ficika ba na magani. “ Ba tace komai ba ta juya ta bar d'akin, dama ba kud'insa suke buk'ata ba, kawai dai ta gaya masa ne a matsayinsa na me jagorantarsu gaba d'ayansu. Umma kuwa bak'in ciki ne yai mugun kama ta da taji wai Shukhura sun yi waya da Nusrat, a yadda bokanta ya sanar mata idan har Shukhura ta kwana a kan gadon nan to sunyi rabuwa ta har abada ita da 'yan uwanta, tsakaninsu kuwa sai dai kallo, ita kuwa Mama na mutuwa, to tabbas ita za ta zamo mahaifiyar Shukhura kuma babu wanda ya isa yai magana akan hakan, dad'inta d'aya ne da ta fuskanci Mama ba ta da lafiya, tsakanin Shukhura da Nusrat kuma za ta zuba ido ta gani. Sun ci sa'a me chamise d'in ya fito, ya yi mata allurar zazzab'i ya bata kuma magun guna, kud'i ya kama 1500 Nusrat ta bashi 2000 ya basu cangin 500 suka kamo hanya suka taho gida. To Alhmdlillh sai jikin nata ya d'anyi sauk'i kad'an, har Nusrat ta had'a mata shayi me kauri ta sha, ganin jikin Maman ya yi sauk'i sai a sannan ta yi tunanin Shukhura har yanzu ba ta kirasu ba, amman gashi ta kira Umma sun gaisa, ta na cikin wannan tunanin sai ga Hidaya ta shigo tace mata tafiya zasuyi, amman zasu fara biyawa gidan Nimha da Shukhura in da sak'on da za'a kaiwa Shukhura a bada, kafin Nusrat ta mik'e ta bawa Hidaya sak'on sai wayar Hidayan ta yi k'ara sai Hidayan cewa ta yi. "Kinga ma Shukhuran na kirana bari muji meye to. “ Ba ta jira me Nusrat d'in za tace ba ta d'aga wayar, ta can b'angaren Shukhura tace. "Hello Hidaya kice a had'o mini duka akwatinana ku taho mini da shi.“ "To, shi kenan za'a taho da su, ga Nusrat za tai miki magana. “ Hidaya ta fad'a don ganin kallon da Nusrat d'in take mata, alamu ne na ta na son magana da 'yar uwar ta ta, k'ittt kike ji Shukhura ta kashe wayarta mamaki gaba d'aya ya kama su, a haka Nusrat ta shiga had'awa Shukhura duka akwatinanta da abubuwan da ba'a rasa ba, suka samo yara duk suka fita da su aka zuba a mota, kana sukai sallama da su Hidayan Nusrat tace. "Ku gaishe mini da Shukhuran ku gaya mata Mama ce ba taji dad'i ba." A tunanin Nusrat idan aka cewa Shukhura Mama ba taji dad'i ba za ta kira waya, in ma fishi take da ita ko tai mata wani laifin da ba ta sani ba ai ta kira layin Maman ta ji, amman har dare Shukhuran ba ta kira ba, ganin yadda duk Nusrat d'in ta bi ta damu yasa Mama tace. "Bani wayata na kirata. “ Saboda tun d'azu Mama tace ta kirata tak'i, saboda ta na ganin kamar ta na da dalilin da yasa tak'i nemansu gara su d'an d'aga mata k'afa su gani. “ Ringin d'aya Shukhuran ta d'aga da murnarta tace. "Hello Ma.......“ Cak taji maganarta ta tsaya ta kasa furta Maman da take buk'atar fad'a, Mama ji tayi gabanta ya yanke ya fad'i a hankula ta furta. "Innalillahi wainna ilaihir raji'un.“ Kafin taji saukar kukan Shukhura a kunnenta. "Shukhura lafiyarki kuwa?“ Cikin kuka tace. "Nima ban san me ke damuna ba, daku na kwanta a raina da ku kuma na tashi, tun da mukai sallar asuba nake son kiran wayarku amman na k'asa, sai na ji ana rad'a mini a kunnena wai ke ba mahaifiyata bace, Umma ce mahaifiyata ko kuma ace su Yayarmu ba 'yan uwana bane Nimha ce kad'ai 'yar uwata, na san Yayarmu ta damu sosai amman wallahi ko muryarta ba na son jin, ina cikin damuwa zuciyata ta na mini zafi, da na san haka auren zai zo mini da babu abinda zai sakani yinshi. “ Ta na kawowa nan ta fashe da wani matsanancin kuka, Mama kuwa Innalillahi kawai take ambata a zuciyarta, yayin da Nusrat duk ta na jin abubuwan da Shukhuran ta fad'a, had'a kanta tai da guiwa ta fashe da kuka me ciwo, 'yar uwarta da take sonta fiye da son da takewa kanta yau itace ta furta ba ta son jin muryarta, me yake shirin tunkaro rayuwarsu ne, waye me buk'atar rusa Katangar farin cikin da suka dad'e da ginata a zuciyoyinsu? Majina Shukhura ta jaa taci gaba da cewa. "Mama kicewa Umma me mukai mata take son rusa rayuwarmu gaba d'aya, in wani abu mukai mata sai mu nemi yafiyarta, na san dai itace ta shiga tsakaninmu saboda da sassafe ita na fara kira na gaisar, bayan ko anan cikin gidan ba kullum nake gaisheta ba. “ Numfasawa Mama tayi tace. "Umma ba ta isa ta miki komai ba Shukhura, ki saka hakan a ranki, babu wani abu wanda yake faruwa a rayuwa face dole sai da wani zare da ya haddasa hakan, kuma bama iya ganin zaren, shi wannan zaren shi ake kira ZANEN K'ADDARA. Dan haka kada ki kuma danganta abinda ya same ki da wani d'an adam, duk abinda ya sameki to ki tabbata yana cikin k'addararki, ki kuma kai kukanki ga Ubangiji domin shi kad'aine zai baki ikon cinye jarabawar da yai miki har ya yaye miki abinda ke damunki, yanzu kije kiyo auwala ki d'auki qur'ani ki karanta za kiji sanyi a ranki, maza jeki, Allah yayi miki albarka, ki kuma daina wannan kukan.“ Muryarta can k'asa tace. "Tom“ Mama ta kashe wayar ta lumshe idonta kana ta bud'esu akan Nusrat da ke gurshek'an kuka...... Jiya ba ku jini ba, chargi ne ban samu ba wutarmu ta lalace, gobe da jibi ba lallai ne ku jini ba saboda muna hidimar biki. 300 za ku biya domin samunsa cikin sauk'i. 0567838462 NABABA FADILA SHU'AIB GTBANK In kuma katin wayane ku turo ta wannan layin, shaidarki ta biya ma ki turo cikinta. 09037093702 In katin wayane 400 zaku biya. Allah ka k'arawa mahaifanmu lafiya da nisan kwana, Amin. #N.W.A #Team KTG #Son so fisabilillah[10/8, 3:42 PM] Binta Lawan: *BEBE'ARTH* 28/8/2020 Wattpad@Rashuna *KATANGA* _Ina matuk'ar godiya ga Allah (S.W.T) da zai ba ni ikon kawo muku wannan littafi mai suna KTG, ina fatan yadda zan fara cikin yalwatacciyar lafiya na kammalashi haka, Amin summa Amin_ _Sak'on gaisuwa ga 'yan uwa da abokan arzik'i, da kuma dukkanin masoyana na kusa da nesa, ina kuma fatan za ku bani had'in kai cikin wannan littafin, kalma d'aya kawai zan gaya muku, alk'alamin ya fi mashi tsini, kuyi k'ok'ari kui nitso ku ninkaya cikin wannan sabon alk'alamin mai suna *KATANGA*_ _Hak'k'in mallaka:_ *RABEE'AH SHU'AYB NABABA* (RASHUNA) ____________ *ONE* _Bismillahir rahamanir rahim._ *SHIMFID'A* Malam Ahmadu an haifeshi a garin Zaria, asalin malantarsa ya gadota ne a gurin mahaifinsa Malam Buba, kasancewar kuma tun ya na yaro mahaifiyarsa ta rasu, tare ya rayu da mahaifinsa har sai da ya yi aure da matarsa Asabe sannan Allah ya karb'i ran malam Buba, daga nan Malam Ahmadu ya ci gaba da jan ragamar mahaifinsa ta malamta. 'Ya'ya uku Allah ya azurtasa da shi, Abdullahi, Maryam sai autansa Shamsu, Abdullahi shine ya gado mahaifinsa amman kuma ba a iya malamtar ya tsaya ba ya na da shago a kasuwa da yake sayar da kayan awo. Malam Ahmadu shine ya zab'awa Abdullahi mata, 'yar amininsa ce k'ud da k'ud da Allah ya karb'i ransu shi da matarsa shekarun baya da suka wuce, kasancewar gidan nasu gidan yawane, kuma auran zumunci akayi tsakanin mahaifan nata, haka take ta watan gari riya a cikin gidan sai uwar bauta da take musu, tausayinta da duba maraicinta da amuntakar da ke tsakaninsa da mahaifinta hakanne yasa ya nemawa Abdullahi auranta, Abdullahi baiyi musu ba kasancewar ya yaba da d'abiunta kuma ta na yawan burgeshi a duk sailin da zasu had'u hakan yasa ya karb'i tayin auranta da hannu bibbiyu. A gurin Asabe wacce yanzu suke kira da Iya aka fara samun k'alubale, inda ta yi tsalle ta dire akan d'anta ba zai auri 'yar makafi ba, kasancewar mahaifanta duk makafi ne, shikuwa Malam Ahmadu yace ta yi kad'an ta hana wannan auran, idan har taga ba'ayi sa ba to tabbas babu ransa a Duniya. Abdullahi da Maimuna sun aminta da juna sosai ya yin da suka fad'a zazzafar soyayya nan da nan magabata suka shiga lamuran nasu, a lokacin ne kuma wanda yake neman auran Maryam me suna Yusuf ya fito, a kano yake a zaune aiki ne ya kawosa zaria, tun ganin farko da yaiwa Maryam ya aminta da ita, bai fara zuwa zance ba sai da Malam ya yi masa izini, daga bisani kuma yace ya turo magabatansa. An tsayar da ranar auran Abdullahi da Maryam lokaci guda . Anan cikin gidan, Malam Ahmadu ya yanki gefe ya yiwa Abdullahi gini, d'akuna uku ne maka² abinsa a wadace, ya yi musu kuma k'ofar gurinsu da ban, sannan kuma ya had'a masa lefe dai-dai da zamanin da suke ciki. Ansha shagalin biki kafin a kawo amarya sashinta, ita kuma Maryam aka kaita unguwar Sabon gari. Lafiya lau zaman Abdullahi da Maimuna yake babu wata matsala ko d'aya, Malam ya d'ebo soyayyar duniya ya d'orawa surukar tasa, kullum in zai shigo gida da abinda zai aika mata da shi, ya yin da Iya kuwa ta bi ta tsaneta, ko kad'an ba ta sakar mata fuska kyara da tsangwama shine tsakaninsu. Wata d'aya da bikinsu Allah ya azurtata da samun juna biyu, tattali da kulawa fiye da wacce take samu ada Malam yake mata, idan ya fita duk abinda ya san me ciki na sha'awa shi yake siyo mata, Iya kuwa tayi ta sababi a tsakar gida ta na masifar ga d'iyarsa can ta na da juna biyun amma ba ya ta tata ya tare a bayan sirika, ya taka k'afa ma yaje ya gano d'akinta baije ba don tsabar tab'ewa da lalacewa, ci kanki kuwa Malam ba yace mata sai dai yai ta murmushi idan ta na yi ya nai mata uzurin k'wak'walwarta ta goce. Cikin Maimuna na shiga wata tara cif, ta haifi kyakkyawar yarinyarta sankace ciya, da hak'oranta guda biyu na k'asa, tsakanin Abdullahi da Malam ban san wanda ya fi wani farin ciki ba, Malam fad'i yake an haifar masa jika 'Yar baiwa, mutane kuwa da wanda Maimuna ta sani da wanda ba ta sani ba sai tururuwar zuwa barka suke, wasu ma don suga hak'oran ne kawai yake kawo su, don duk wanda yazo sai ya d'aga bakin ya gani, sai dai kawai Maimuna ta yi murmushi. Iya kuwa ko lek'owa taga jikarta ba ta yi ba, illa ma bak'in ciki da take kamar ranta zai fita, saboda yadda taga malam ya na rawar k'afa ya samu jika 'Yar baiwa, don har ya siyo raguna biyu tik'a² ya tirkesu bakin nan yak'i rufuwa, Iya kuwa tace. "Inma za ka daina farin ciki ka daina, shawara nake baku ku d'auki 'yar nan ku kaita bakin ruwa don wallahi 'yar aljanu ce ba 'yar baiwa ba. “ Murmushi kawai Malam ya yi baice da ita komai ba don ya san bak'in ciki ne ya taru yai mata yawa. Ansha shagalin suna yadda ba kwa zato, yarinya taci sunan babar Malam AYSHA, Maimuna tace a dinga kiranta da NUSRAT, yayin da Malam ya d'ebo soyayya,tattali gami da kulawa ya aza akan 'Yar baiwa. Wata d'aya tsira Maryam ma ta haifi 'yarta mace taci sunan babar Yusuf RABEE'AH suke kiranta da HIDAYA. Watan Nusrat uku a duniya Iya ta matsawa Ahmadu number sai ya k'ara aure, wata bazawara ce nan mak'otansu da take shigo mata, mijinta mutuwa ya yi kuma mai bala'in kud'i ne, siyayya take yowa Iya sosai da haka ta siyeta, don dama burinta kenan ta tirsasa d'an nata ya aureta, don ta tareshi da buk'atarta ya yi mata kaca² hakanne yasa ta biyo ta gurin Iya. Don a samu zaman lafiya Malam yacewa Abdullahi ya aureta, itama ya bi zab'inta,ko a samu k'iyayyar da takewa Maimuna ta ragu, don fad'i take yaiwa mahaifinsa biyayya amman ita saboda bai d'auketa a bakin komai ba ya watsa mata k'asa a ido ta ya ya kwa za ta k'aunaci Maimuna? Tun sanda aka saka ranar tarewar Bulki Malam da Abdullahi suke kwantarwa da Maimuna hankali ita kuma ta nuna musu hakan ba komai bane dama ai namiji mijin mace hud'u ne. D'aki d'aya shi ya zama na Maimuna, d'aya na Abdullahi d'ayan kuma na Bulki. Ranar juma'a aka d'aura auransu kuma a ranar ta tare, farin ciki gurin Iya ba'a magana kamar ta zuba ruwa a k'asa ta sha, tunda take ba ta tab'a taka gurinsu ba sai a ranar da aka kawo Bulki. To zamansu dai ga shinan da dad'i babu dad'i a haka rayuwar take juyawa. Shekarar Nusrat d'aya Maimuna ta sake haihuwar mace wacce taci sunan mahaifiyar Maimuna SAFIYYA suke kiranta SHUKHURA, wata uku tsira Bulki ma ta haifi 'yarta mace wacce taci sunan Iya na gaskiya ZAINAB suke kiranta da NIMHA, anan fa Iya ta baje kolin gata da soyayya, fad'i take yanzu ne aka haifa mata jika. Tun haihuwar Shukhura sai da Maimuna ta shekara biyar kafin ta haifi wata macen aka saka mata NA'IMA suke kiranta da YUSRA, ita kuwa Bulki ba ta sake haihuwa ba tun daga kan Nimha. Malam yadda kuka san bai da wata jika sai Nusrat, komai ya samu 'Yar baiwa, kayan ciye² kuwa sai ta rage ake samwa k'annenta, ta shak'u da kakan nata fiye da zatonku masu karatu, shima kuma ta shiga ransa sosai da sosai, ya na bata kulawa ne ba wai don fifici ko wani abuba, sai dai shi a ganinsa dole ne jikanka na fari ya banbanta da sauran, saboda gaba d'aya soyayyar da kakewa d'an naka kake 'yebowa ka aza a kansa. Amman a gurin Iya da Bulki cin fuskane kawai, don a nuna ba'a son Nimha, hakan yasa suma suka d'auki dukkanin tsana suka d'ora akan Nusrat. Nusrat Fara ce, amman farinta mai duhu ne, fuskarta siririya ce mai d'auke da siririn dogon hanci, idanuwanta suna da girma matsakaici masu shape d'in k'wan k'walati, cikin idonta fari ne tas ruwa ya kwanta a cikinsa mai maik'o, k'wayar idonta kuwa bak'a ce me silkin brown a ciki, bakinta d'an madai daici ne haka zalika lab'b'anta basu da wani tudu, ko ya ta motsa bakinta wani siririn dimple ne ke bayyana a gefen kumatunta na tsaye wanda yake k'ara fito da zallar kyahunta. Shukhura kuwa fara ce k'al, suna yanayi da Nusrat, amman ta fi Nusrat kyau, kina ganinta kai tsaye za ki kirata kyakkyawa, saboda ita ko ba tai murmushi ba kumatunta a lotse yake, kuma nata irin na kwance ne. Yusra ma fara ce kamar Shukhura, itama ta na yanayi da su, amman kuma ba ta da dimple. A yanzu shekarun Nusrat goma sha biyar a duniya, ta na sss1, su Shukhura kuma shekarunsu goma sha hud'u suna jss 3 auta Yusra kuma shakarunta tara a duniya ta na aji hud'u a primary. Allah ya yiwa Malam rasuwa shekaru hud'u da suka wuce bayan ya yi jinya kad'an, kowa ya ji babu dad'i domin anyi babban rashi mai girma, musamman Nusrat, bayan mutuwarsa ne kuma soyayyar da Abdullahi wanda yanzu suke kira da Baba yakewa Nusrat ta fara bayyana, don har ga Allah ya fi k'aunarta ya na b'oyewa ne saboda kada ya kuma janyo mata bak'in jini. mutum ne me wadatar zuciya, ba wani k'arfi ne da shi ba sai dai rufin asiri na Ubangiji, don sun wuce cin yau da na gobe a gidansa, haka zalika bai bar iyalansa a wulak'ance ba, a ko da yaushe za ka samesu cikin kyakkyawar kamala. Shamsu ya yi aure da matarsa Fiddausi da d'iyarsu Amima sa'ar yusra, sunanta na gaskiya Zainab, shima Iya ya yiwa takwara, a kaduna suke a zaune a saboda anan ne yake aiki, ya ninka yayan nasa sosai a fannin dukiya wanda k'arara Iya ke nuna banbanci tsakaninsu da Baba. Aunty Maryam kuma mijinta ya koma kano da aiki don haka ya d'ebe su suka koma kano da zama, 'ya'yansu hud'u yanzu, Hidaya, Abdul, Hibba, Abbas, suma sosai Iya take ji da su saboda suma mahaifinsu na da kud'i, kuma anai mata aike akan kari. *Wannan kenan* 300 za ku biya domin samunsa cikin sauk'i. 0567838462 NABABA FADILA SHU'AIB GTBANK in kuma katin waya ne ki turo ta wannan layin, shaidarki ta biya ma ki turo cikinta. 09037093702 In katin wayane 400 zaku biya. Garab'asa gareku masoyana, duk wacce ta sayi wannan littafin za ta sami wanda zan rubuta gaba kyauta, ban yadda ki sayi littafina ki dinga turawa gruop ba, in hakan za kiyi ki sameni a layina muyi magana. Allah ka k'arawa mahaifanmu lafiya da nisan kwana. #Team KTG #N.W.A [10/8, 3:42 PM] Binta Lawan: *BEBE'ARTH* Wattpad@Rashuna *KATANGA* ____________ *TWO* Yau ta kama lahadi, duk da suna cikin hutun makarantar boko, su Nusrat duk sun tsefe kawunansu zasu kitso, sai da Nusrat ta fara wanka ta yiwa Yusra ma ta wanke mata kanta ta taje ta shafe mata shi da mai sannan suka shirya zasu tafi, kallon Shukhura Mama ta yi da ta saka hijabi zasu tafi tace. "Ke yanzu ba za ki wankan ba haka za ki bisu?“ Sai da ta fara turo baki gaba kana tace. "To Mama nan da nan d'in sai na yi wanka, abinda yanzun nan za'a mana mu dawo. “ "Allah ya shirya. “ Mama kawai tace ta na mik'awa Nusrat kud'in kitson nasu had'e da fad'in. "Ta fara yi miki kitson, kuma tai miki manya don kinsan yadda yawan kanki yake, kuma ke zan barwa girkin dare don fita zan yi, saura kuma kice a fara yiwa Yusra don na san hali. “ Murmushi Nusrat ta yi, bayan ta saka hannu biyu ta anshi kud'in kana tace. "Mun tafi.“ Maman tace. "Allah ya tsare, ku dai yi addu'a kafin ku fita. “Tace. "Amin, tom insha Allah.“ Tare da jan hannun Yusra suka bi bayan Shukhura da ta fita tun d'azu. Har sun d'an gota gurin Iya ta hango giftawarsu da sauri ta k'walowa Nusrat kira. "Ke ke A'i zo nan. “ Da yake haka take kiranta tun ma Malam na raye, juyowa Nusrat ta yi, Yusra ta turo baki gaba tace. "Wallahi na san aiki za ta sakaki, kawai kizo mui tafiyarmu mu rabu da ita.“ Murmushi Nusrat ta yi tace. "Bara dai naje na ji kiran da take mini.“ "Tak'i ta rabu da ni d'in, shegiya ifrituwa me zunb'utun baki. “ Suka jiyo muryar Iya daga ciki, kuma turo baki Yusra ta yi ta na hararar gurin kafin ta fice waje da sauri, Nusrat kuma ta nufi gurin Iyan ta na murmushi. Gyaran d'aki tace tai mata da wankin band'aki sai 'yan tsunmokaranta ma da tace ta wanke mata. Kallon Shukhura Nana me kitso ta yi tace. "Ina su Yayar taku?“ "Ga sunan suna hanya. “ "To shiga ciki, gani nan bari na k'arasa sharar nan. “ Rufe bakinta kenan Yusra ta yi sallama, kallon ta Shukhura ta yi bayan ta amsa sallamar ta ta tace. "Ina Yayarmun?“ "Ba Iya ce ta kirata ba, har ta na ce mini ifrituwa. “ Wani haushi ne ya kama Shukhura, ta zura takalminta ta fasa shiga d'akin ta fice a fusace Yusra ta biyo bayanta. Kamar an jefota ta shigo ta na kallon Nusrat da ke zubar da shara. "Sannu" Tace mata, kafin ta shige zuwa gurin Iya, iya na ganinta ta d'aure b'arin goron da ta b'antara a gefen zaninta kana tace. "To rasa kunya b'eran tanka, kinzo kimin rashin kunyar taki ne? “ Kar katar da kai Shukhura ta yi tace. "Ashe 'Yar aljanu na da rana tun da har an iya sakata aiki, me yasa ba ki kirawo 'yar lelen taki tai miki ba sai ita za ki saka, amma in abu zaki bayar babu wanda ke gabanki sai Nimha, amman in aikine sai wacce kika raina, don kin san Nimha ko tsintsiya ba za ta iya d'aga miki ba. Bayan kuma kitso zamu je kina gani kuma Mamanmu na zaman jiranmu“ "Tunda dai ba ke na saka ba, ki shige ki bani guri, kiyi can da rashin kunyarki. “ Cewar Iya "Waa aini kin san abinda bazai tab'a yuyuwa bane, don wallahi bazan bautawa wanda bai san ina yi ba, in cin mutumci ne ya taso azo a tarkace mini, lalalala wallahi, itama ita taga za ta iya.“ "Ni kikewa cin mutumci Safiya, Allah ya dawo da Audu, wallahi za ki gane Ubanki na haifa. “ "Amin, ya dawo d'in ki gaya masa, wallahi duka d'aya yamin kinsan sai na bi ta inda zan rama, Allah ya baki sa'a. “ "Wai da sa'ar ki kikeyi ne Shukhura?“ Cewar Nusrat ta na kallonta, ba ta bata amsa ba ta fice ta na zunb'uro baki, Iya kuwa k'ifi² ta yi da ido tunowa da ta yi sanda ta saka Nusrat a gaba ta na zaginta Shukhura ta amshe ta hayayyak'o kamar za ta daketa har sai da Mama ta fito ta kikkifawa Shukhura mari, shine Baba ya na dawowa Iya ta kwashe ta gaya masa, aikwa ranar Shukhura ta sha duka gurin Baba, ita kuwa ta d'auki aniyar wallahi sai ta rama akan Iya, sai da ta bari duhu ya yi ta kad'a karkashinsu me yauk'i taje ta zuba a band'akin Iya,don ta na da tabbacin yanzu za ta fito ta shiga band'akin ta lab'e a bayan k'ofa, Iya na shiga ta yi sufa ta fad'i Shukhura ta fito ta na ta k'yak'yata mata dariya, tace mata kad'an ta gani muddun ta na sakawa Baba na dukanta, Iya kuwa jiki yai tsami da k'yar ta iya mik'ewa. "Yanzu Mama kina kallo ga Iya can ta saka Nusrat aiki.“ Shukhura ta fad'a ta na turo baki gaba. “ "To meye, don ta sakata aiki?“ Mama ta fad'a ta na cigaba da tankad'en da take. "Amma Mama kefa kikace a fara mata kitson saboda za ki bar mata girki.“ "Yanzu kuma na fasa ba, kije ke a fara miki sai ki baro Yusran a can in Yayar taku tazo sa taho tare sai ki karb'i girkin na samu na fita. “ "Amma Mama....“ Dakatar da ita Mama ta yi had'e da fad'in. "Ban san jin komai ki shige kije kiyi abinda na saki. “ Fita ta yi ta na tutturo baki Mama ta girgiza kai had'e da fad'in. "Allah ya shirya. “ Sai da Iya ta kinta tanci dawowar Baba ta fito babban tsakar gida ta k'wama kujera ta na jiran dawowarsa, aikwa ta na jin sallamarsa ta saki kuka me k'arfi, a gigice ya nufota ya na tambayarta. "Lafiya Iya, me ya faru kike kuka haka?" Face hanci Iya ta yi tace. "Wai ni yau A'i za ta kalli tsabar idona ta zageni ta uwa ta uba. “ " 'Yar baiwa.“ Baba ya k'wallawa Nusrat kira, Nusrat da ke d'aki tun da ta dawo daga kitso kanta ke ciwo shine ta nemi guri ta kwanta, ta na jiyo abinda Iya ke cewa Baba gabanta ya yanke ya fad'i, da ta ji kwa ya k'wallo mata kira nan da nan idonta ya yi rau-rau zai fidda ruwa, a hankali ta mik'e ta fito ba tare da ta amsa kiran ba, kallonta Shukhura ta yi da ke kwashe tuwo ta cika k'atuwar kula ta kai d'akinsu, tace. "Kinga dai da abinda ta saka miki ko? kuma wannan ba shi zai hana gobe idan tace yimin kaza kiyi mata ba. “ Ba tace mata komai ba sai juya idonta da tayi da ya fara fitar da ruwa ta nufi tsakar gidan, Shuk'hura kuwa taci gaba da kwashe tuwonta ta na mamakin sanyin hali irin na Nusrat, ta yi k'wafa a hankali, a ranta tace. 'Iya kenan, ai gara ki tab'ani akan ki tab'a Yayarmu wallahi, don ba ki son son da nake mata bane.' Baba na ganin ta taho a sanyaye ya saki murmushi had'e da fad'in. "Taho mana 'yar baiwa. “ Ganin murmushi akan fuskar Baban nata yasa ta samu k'arfin guiwar k'arasawa gareshi, bak'ar ledar hannunsa ya mik'a mata, me d'auke da d'ata manya-manya kasancewar yasan ta na matuk'ar son d'ata, kana yace. "Ga masoyin naki.“ Murmushi me sauti ta saki tace. "Na gode Babana. “ Baki galala Iya ta saki ta na kallonsu daga bisani ta tafa hannuwa tace. "Yau naga lalacewa ni Asabe, yanzu ina gaya maka abinda yarinyar nan ta yi mini amma kai d'ata ka d'auka ka bata, gani ni wacce na yi silar zuwanka duniya ka san da cewa ina mutuwar son ka'za amma baka tab'a siyowa ka bani ni kad'ai a gidan nan ba, sai dai ka siyo gaba d'aya aci, amman ita da yake shafi da mai ce ka ware ta cikin 'yan uwanta uku, ture biyunma tunda su cikinsu d'aya ai ko Nimha ka siyowa don gudun fitina.“ "D'atan da na siyo mata na tabbata ba za ta cishi ita kad'ai ba, rabawa zasui gaba d'aya da ita da 'yan uwanta, zancen kuma Nusrat ta zage ki wallahi Iya ko jikina duk kunne ne bazan tab'a yadda za ta iya zaginki ba, ko da kuwa dukan mutuwa kikai mata a cikin gidan nan, bare kuma na san halinta ba sawa ba fitarwa, da dai Shukhura kika ce to tabbas wannan zan yadda amma 'yar baiwa lalala, sai dai kice Shukhura ce ta zageki kikace 'yar baiwa ce saboda.... ”Da sauri Iya ta dakatar da shi da fad'in. 'Ni wallahi bance maka Safiya ba, ko sunanta ban ambata a gurin nan ba in ba yanzu ba, jama'a ko kunji na ambaci Safiya? “ Ta fad'a da k'arfi yadda 'yan ciki zasu jiyo ta, murmushi Baba kawai ya yi ya ja hannun Nusrat sukai ciki. "Kedai Mero kin haifi jarabar aljanu a gidan nan, yarinya ta bi ta zamar muku masifa duk kunfi k'aunarta cikin 'yan uwanta, su kuma hakan ko kad'an hakan ba ya damunsu, wannan wata iriyar musifa ce? Kai kuwa Audu k'atuwar asara ce ta hau kanka don zan iya dafa qur'ani kafi son wannan 'yar aljanun ko nace 'yar ruwa akan ni da na diroka duniya, bacin haka har maganata za ka k'aryata ka zab'i d'iyarka, babu komai ai gobe Shamsu zai zo garin, Allah sarki d'an albarka na san gobe miyarmu da ka'ji zan cisu har na ture, don ni ina jin idan yazo ma tattara kayana zan na bisa, don wallahi na gaji da cin shinkafa 'yar hausa da tuwon garin masara kullum suna cushe maka a ciki, don na ji ana rad'e rad'en tuwon masara gini yake a cikin mutum, haka kawai na zauna naje na kashe kaina tun wa'adina bai cika ba. “ Sai misalin k'arfe takwas Mama ta dawo, kallon Nusrat da ke kwance ta yi tace. "Ina Mamana, Yusra taci abinci da kika barta tai bacci?” "Cikin gida tace mini za ta shiga tun d'azu, Yusra kuma sai da taci abinci tukunna tai bacci. “ "Lafiyanki kuwa naga kina yatsina fuska? “ Ta tambayeta duk da a ranta mamakin wai Shukhura ce tace ta tafi cikin gida, bayan ba k'aunar zuwa gidan take ba, aike ma da dole take shiga. "To ki tashi ga fura na taho miki da ita kisha sai ki sha magani.“ Da hanzari ta mik'e don dama yunwa take ji kuma har ga Allah ba ta k'aunar cin tuwon donma ta d'an ci d'atan da Baba ya kawo mata duk da wasu sunce shima ya na faifaye ciki, ita kuwa Mama sanin halin d'iyar ta ta yasa ta yo mata guzurin furar. Sauke idanuwanta ta yi akan kular tuwon da Shukhura ta ajiye, a fili tace. "Allah ya shirya mini ke mamana. Maza Nusrat ki gama kije ki kira mini ita. “ Ta na rufe bakinta ta jiyo sallamarta suka amsa mata. "Laa Mamanmu kin dawo ashe? sannunki da dawowa. “ Fuska a had'e tace. "Yauwa, me kika je yi cikin gida? “ "Nifa ba cikin gida nace mata zanje ba, gidan su Farha nace mata za ni kallo.“ Takai k'arshen maganar ta na kallon fuskar Nusrat. "Ban hana ki zuwa kallo ba?to da Babanku kawai zan had'aki na huta, Ke kuma ai ga shinan kin rufa mata asiri ta tonawa kanta. “ Takai k'arshen maganar ta na kallon Nusrat, yayin da ita kuma ta saki murmushi. "Kiyi hak'uri Mamanmu bazan sake ba. “ "Sau nawa kina fad'in haka? “ "Allah da gaske nake Mamanmu daga wannan bazan sake ba. “ "To wancan uban tuwon da kika ajiye da fatan abincinki ne na sati guda ko?“ "Haba² Mama, sai kace wacce uwarta ta tsine mata duniya ta juya mata baya zan jera sati guda ina cin tuwo, tuwonma ba sabo za'a dinga yi mini ba. “ Mama ta so yin dariya amma ta kanne tace. "Koma me zaki ce kice, amma wancen tuwon sai kinyi sati kina cinsa a gidan nan tun da ke kunnenki na k'ashi ne ba ya jin magana, bacin sau nawa zance ki daina cika mini kula kina kawo mini d'aki? “ Sai da ta fara turo bakin nan gaba kana tace. "To kina dai kallo duk ran girkinta sai ta cika kula fam ta kai d'aki, bacin daga ita sai 'yarta d'aya kamar rai, mu kuwa ta milliro mana, ta cikawa Baba da sirikarta kwano, nima kuwa yau na rama na millira musu na millirawa Iya ma, Baba kuwa na cika masa kwano har ya na zuba. “ Salati Mama ta yi ta saki baki ta na kallon Shukhura. "To don ita ta na cika kula ta kai d'aki ita ta shafa, sune mayunwata ba mu ba, ga shinan yanzu kin sakani a bakin duniya, tijarar Iya ma kad'ai ta isheni, don cewa za tai ina sani na baki girkin shiyasa har ga Allah ban son na bar miki girki na fita. “ "A to don wallahi muddun ni nai girki bazan fasa ciko mana kula na kawo d'aki ba, ko ba za muci ba sai dai mui asararsa. “ "Me kika ce?“ Mama ta tambayeta kasancewar k'asa² tai maganar. "A'a cewa na yi kiyi hak'uri bazan kuma ba. “ "To zo ki fice mini da kular, kije ki k'ara musu tuwon.“ Ta na jin haka ta saki k'ara. "Waishhhhhh Mama kashi² ina zuwa ta fice da gudu zuwa ban d'aki, murmushi Mama ta yi a ranta ta na nemawa Shukhura shiriya ta d'auki kular tuwon ta fita, murmushi ma Nusrat keyi tun fara dramar Maman da Shukhura, don dama sun riga da sun saba...... 300 za ku biya domin samunsa cikin sauk'i. 0567838462 NABABA FADILA SHU'AIB GTBANK In kuma katin waya ne ki turo ta wannan layin, shaidarki ta biyama ki turo cikinta. 09037093702. In katin wayane 400 Za ku biya. Garab'asa gareku masoyana duk wacce ta sayi wannan littafin za ta sami wanda zan rubuta gaba kyauta, ban yadda ki sayi littafina ki dinga turawa gruop ba, in hakan za kiyi ki sameni a layina muyi magana. Allah ka k'arawa mahaifanmu lafiya da nisan kwana, Amin. #Team KTG #N.W.A [10/8, 3:42 PM] Binta Lawan: https://chat.whatsapp.com/L7ZWZtJoVg39WGbG36r78I. Pls share *BEBE'ARTH* Wattpad@Rashuna *KATANGA* ____________ *THREE* Ashe ba kallo Shukhura taje ba, can bakin titi taje gurin me saloon ta siyo farata koraye shar da su, ta biya gurin me zob'o ta siyo, ta sayi cewing gum ta jefa a baki sannan ta yo gida, a wani d'an lokon babban tsakar gida ta ajiye faratan da zob'on kana ta shigo. Sai da ta bari d'aya ta gota ta tabbata a lokacin baccin kowa ya yi nisa ta salallab'a a hankula ta zare sakatar gurinsu ta fice, bayan ta d'auko farar hodarsu, ko tsoron duhun dare ba ta yi, bursuna farar hodar ta yi tun daga fuskarta har wuyanta, ta cire hijabinta sai ta bar wata hula me cibiri cibirin gashi a kanta, rigar jikinta dama ta wani tsohon uniform d'inta na islamiya ne da take bacci da ita. Cikin dabara ta man manna faratan a yatsunta da chewing gum, ta d'aga jarkar zob'on nan ta shanye ta bar d'an guntu a ciki, nan da nan bakinta ya yi jajir, ta guntsi ragowar a bakinta, turmi ta taka ta zira hannunta ta saman k'ofar d'akin Iya a hankula ta zare sakatar kana ta tura ta shiga ta mayar ta rufe, kallon Iya da ke bacci akan gado ta yi, sakamakon haska 'yar k'aramar cocilan d'in da ke hannunta da ta yi a ranta tace. 'Za ki gane kurenki ne.' Kan ruwan cikinta ta hau ta zauna, cikin bacci Iya ta ji masifar nauyi ya ziyarceta, a hankula ta bud'e idanuwanta duk a tunaninta madannin dare ne ya danneta, ido biyun da ta yi da Shukhura nan take wani mugun tsoro ya kamata ta bud'e baki za tayi ihu Shukhura ta yi saurin toshe mata baki da wani tsumma da ta yayibo a gefenta, cikin wata iriyar murya me ban tsoro tace. "Kada ki mana ihu a nan, in ba haka ba zamui daga daga da namanki. “ Nan da nan jikin Iya ya fara rawa kar kar ta fara biya duk wata addu'a da tazo bakinta, son tashi take amma gaba d'aya ta k'asa tashi, hannu Shukhura ta Saka ta karto gefen fuskar Iya had'e da juyar da idanuwanta, rintse ido Iya ta yi kafin ta ji saukar muryar Shukhura a kunnuwanta. "Al'quran kika kuma tsangwamar Nusrat a cikin gidan nan sai mun cire miki k'afa d'aya da hannu d'aya, mu kuma maidar miki bakinki k'eyarki, sannan mu d'aukeki zuwa cikin ruwa, kima gode Allah kin fara manyanta da wallahi yau sai mun sakaki murmushi da hak'ori d'aya.“ Iya firgita Iya ta firgita, wani mugun tsoro ne ya kuma shiga jikinta ko k'wak'k'waran motsi ta kasa, ta na san magana amman ba dama saboda ta toshe mata baki da t'summa kuma ta rik'e da d'aya hannunta, um umm kawai take ta na girgiza kai hawaye na zuba a idonta, tausayi ta bawa Shukhura don tasan ta sha nauyi, don Iya irin siraran tsofaffin nan ne, ita kuwa Shukhura ta na da jiki, d'agata ta yi ta sauka daga kan gadon ta cire hannunta daga bakinta had'e da fad'in. "Kada kuma ki sake ki mana ihu don wallahi zan maidar miki da idonki goshi ki zama mai ido d'aya. “ Ta na maganar ne ta na ja da baya, yayin da Iya tace. "Allah ya baku hak'uri wallahi na daina takura mata, ba iya ita kad'ai ba ma wallahi dukansu na daina shiga harkarsu.“ Wani ihu Shukhura ta yi ta na zaro harshe ya yin da Iya ta yi wani hantsile ta koma k'arshen gado goshinta ya bugi da bango, duk azabar da ta ratsa ta k'wak'wal warta amma haka ta d'inke bakinta saboda tsoron kar ta yi ihu a maidar mata da idonta goshi, ja da baya Shukhura ta ci gaba da yi had'e da fad'in. "Kada kuma ki sake ki juyo sai mun b'acewa ganinki in ba haka ba kuma zamui sama da ke zuwa fadar sarkin aljanu. “ Ta na kawowa nan, ta bud'e k'ofa ta fice, ta taka turmi ta maidar mata da sakatar ta, kana ta d'auke turmin ta mayar da shi mazauninsa, sannan ta d'auki hijabinta ta shige ciki, ta na k'ok'arin mayar da sakata ta ji muryar Baba yace. "Waye nan?“ K'irjinta ta ji ya yi wani irin bugu nan da nan wani mugun tsoro ya kama ta ta fara rawa da bakinta. "Um nice, fitsari na fito naga kamar ba'a saka sakata ba, shine na duba. “ Ta na kawowa nan ta yi saurin fad'awa band'aki don gudun kada ma ya fito ya ganta. Fuskarta ta wanke da sabulu, ta cire faratan ta jefa a shadda, kana ta fito ta koma d'aki, sai bayan da ta kwanta a shimfid'arta wata muguwar dariya tazo mata, fashewa ta yi da dariya sosai ta na hango yadda idanuwan Iya suka firfito gaba d'aya kamar na mayyar da aka kama, wata dariyar ta kuma fashewa da ita, Nusrat da ke gefenta ta farka ta na kallonta a tsorace. 'Anya kuwa babu almutsutsai akan Shukhura kuwa. ' Taji zuciyarta ta jefo mata wannan tambayar kafin ta ji muryar Baba ya na k'walo mata kira. " 'Yar baiwa“ "Na'am Baba. “ Ta amsa, ta tashi ta fita jiki a sanyaye. "Lafiya kuwa nake jiyo dariya a d'akin ku?“ "Wallahi Baba Shukhura ce, kuma ban san me takewa dariyar ba, anya Baba ba za'a nema mata magani ba, ni wasu abubuwan in ta na yi gani nake kamar ba ita kad'ai ba. “ Murmushi Baba ya yi yace. "Shukhura. “ "Na'am.“ Ta amsa cikin muryar shagwab'a ta fito ta na sosa kai. "Me ya sakaki dariya cikin tsohon daren nan? “ Sai da ta fara turo baki gaba sannan tace. "Kawai tuno yadda na tumur mushi hadiza d'azu a makarantar allo na yi, tsokanar Yayarmu ta yi ni kuwa na had'a mata jini da majina ta mik'e da k'yar jiki duk yai tsami kamanninta duk sun sauya bakin nan kamar zunb'utun zakara. “ Ta kuma fashewa da wata dariyar. "To jeki ki kwanta, kinga dare ne kada ki kuma dariyar, kinji Mamanmu. “ D'aga masa kai ta yi, ta koma d'aki, ya bita da idanuwa a zuciyarsa ya na nema mata shiriya, duk da a zuciyarsa shima ya fara tunanin ba ita kad'ai bace, don al'amarin nata akwai ban tsoro, shiyasa ya daina dukanta ko me Iya tace tayi mata, don ya san itama Iyan da laifinta, kuma duk irin dukan da zaiwa Shukhuran ba shi zai hana ta samo ta inda za ta rama akan Iya ba. Duban Nusrat ya yi yace. "Je ki kwanta 'Yar baiwa, zamui maganar da Mamanku da safe.“ "Toh“ Tace had'e da juyawa ta koma d'akin, ta na kwanciya Shukhura ta rungumota ta baya ta na sakin dariya. "Ina sonki Yayarmu, matuk'ar ina numfashi bazan tab'a bari a tab'a mini ke ba na k'yale, da a tab'a ki gara ni a tab'a ni. “ Wasu hawaye ne suka zubo a fuskar Nusrat wa'yenda ba ta san dalilin zubowarsu ba, hannu ta saka ta baya ta rik'e hannun Shukhura gam had'e da fad'in. "Nima ina sonki k'anwata, amma don Allah ki daina fad'a kinji k'anwata. “ "Zan daina, idan har aka daina tab'aki, fatana na saka tsoron ki a zuciyar duk me tab'aki, yadda ko ganinki ya yi sai yai shayin yi miki magana." Ta na kawowa nan ta kuma rungumota a haka bacci ya d'auketa saboda ba ta da wuyar yin bacci, Yusra da ta farka ta jita ba jikin Nusrat ba ta yi juyi ta shige jikinta, hannu Nusrat ta saka ta na shafa kanta, ta na shafo kan Shukhura da d'aya hannun, har lokacin hawaye na zuba a idanuwanta, ta tabbata hawayen k'aunar da 'yan uwanta suke mata ne, kyakkyawar Katanga mahaifiyarsu ta gina musu a zuciyoyinsu na k'aunar junansu, babu ruwansu da k'yashi ko bak'in cikin anyiwa wani abu a cikinsu ba'aiwa d'aya ba, ta na fatan soyayya da k'aunar da sukewa junansu suci gaba da ita har k'arshen numfashinsu, kada Allah ya bawa wani nasarar rusa katangar alak'ar da take ginanna a zuk'atansu. Dubanta ta kai ga mahaifiyarsu da ke baccinta cikin kwanciyar hankali, duk abubuwan da suka faru ba ta san anyi ba, kasancewarta me nauyin bacci, shiyasa ko wani abun Baba ke buk'ata a gurinsu sai dai ya k'wallowa Nusrat kira. A b'angaren Iya kuwa k'wak'wame da bango wani wahalallen bacci ya yi gaba da ita, ba tare da ta shirya zuwansa ba. Washe gari da safe Nimha da taje kaiwa Iya abincin kari, kasancewar girkin Ummanta ne, anan ta samu Iya da kumburarran goshi, gefen fuskarta a karce. "Ayya Iya sannu me ya same ki?“ "Ke dai bari 'yar nan, duhun dare ne irin na damuna, na tashi fitsari na nemi cocilan d'ita na rasa nai shahada na fito haka shine na sha k'asa.“ "Ayya sannu Allah ya kiyaye, ga karin kumallon ki nan.“ Cewar Nimha, daga haka kuma ta juya ta fita kafin Iya tace. "Amin. “ Nimha na zuwa ta gayawa Ummanta abinda ya samu Iya, tab'e baki Umman ta yi had'e da fad'in. "Wa ya sani ma ko karkashin aljanar yarinyar cen ta kuma kad'awa ta zuba mata, ni ban tab'a ganin tak'adiriyar yarinya irin Shukhura ba, Iya na cewa Nusrat 'yar aljanu ai Shukhura ce 'yar aljanu ba Nusrat ba.“ Maganar da Umma ta yi kaf a kunnen Shukhura suka sauka, wani murmushi ta yi a ranta tace. 'Allah ya had'amu za kwa kiyi kallon tak'adiranci.' Kowa na gidan sai da ya shiga ya duba Iya, Nusrat da Shukhura a tare suka shiga duba ta, abinda ya bawa Nusrat mamaki ganin Iya ta kirata da Nusrat abinda tsawon rayuwarta ba ta tab'a kiranta da shi ba, sai dai ta kirata da Ai, ba ma za tace Ayshan ba, duk don Malam ya ji haushi. Sannan kuma har suka fito ba ta sanyata aiki ba, kasancewar duk sanda ta shiga gurin ba za ta fito ba sai ta moreta ko ya ya ne, kuma ta na kallon Shukhura ta na ta sunkui da kai ta na matse dariya, shine da suka koma d'aki ta dubi Shukhuran tace. "Wai dariyar me kike ta matsewa ne a d'akin Iya? “ "Yo ba dole na yi dariya ba, kinga kuwa goshinta kamar mulmuleliyar daddawa sai shek'i yake. “ Ta fashe da dariyar da ke cinta tun d'azu. "Allah ban yadda da ke ba Shukhura, duk yadda akai ta dalilinki Iya ta ji ciwon nan. “ " To ni me ta mun da zan saka ta ji ciwo? “ Ta fad'a ta na d'an turo baki gaba. "Kefe kika ce sai kin saka tsorona a zuciyar duk me takura mini, kuma yau kallon da Iya ta yi mini ya bam bamta da wanda ta ke mini a kullum.“ Rik'o hannuwanta Shukhura ta yi had'e da fad'in. "Tabbas 'Yar baiwa ce ke Yayarmu.“ Kana ta shiga labarta mata yadda sukai da Iya ta na dariya, murmushi Nusrat ta yi tace. "Tabbas Iya tai namijin k'ok'ari da ba ta sume miki ba, don in nice wallahi sumewa zan yi, a gaskiya kin d'au hak'k'in 'yar tsohuwa, don ta tsorata sosai tun da gashi ko labarin ainihin abinda ya faru ba ta bayar ba.“ "Wallahi ba wani hak'k'in ta da na d'auka, in hakane ita sau nawa ta na d'aukar hak'k'unanmu. “ Girgiza kai Mama ta yi, a kwance take duk a tunaninsu bacci take, duk abinda Shukhuran ta fad'a ta jishi, kuma ta na nemawa 'yar tata shiriya, don Baba yace da kansa zai dingai mata rubutu ta na sha, don abin nata ya fara yawa duk abinda akai mata tace sai ta rama ko ta halin k'ak'a. "Kya ci gidanku, bari Babanku ya dawo sai na gaya masa, kuma ki tashi kije yau ke za ki mata shara ki wanke mata band'aki. “ Zunb'uro baki gaba tai ta mik'e, don in ba ta ta shi ba ta san Mama na iya jefo mata duk abinda ke kusa da ita, bayan fitarta Mama ta yi tunanin may be taje ta kumai mata wata muguntar don haka ta shiga k'wala mata kira kafin ta tashi ta bi bayanta....... 300 za ku biya domin samunsa cikin sauk'i. 0567838462 In kuma katin wayane ku turo ta wannan layin, shaidarki ta biya ma ki turo cikinta. 09037093702 In katin wayane 400 zaku biya Garab'asa gareku masoyana duk wacce ta sayi wannan littafin za ta sami wanda zan rubuta gaba kyauta, ban yadda ki sayi littafina ki dinga turawa gruop ba, in hakan za kiyi ki sameni a layina muyi magana. Allah ka k'arawa mahaifanmu lafiya da nisan kwana, Amin. #Team KTG #N.W.A [10/8, 3:42 PM] Binta Lawan: *BEBE'ARTH* Wattpad@Rashuna *KATANGA* ____________ *FOUR* Washe gari da safe misalin goma da rabi, zaune suke suna cin jolof in taliya a babban tray, kasancewar Baba ba ya nan ba a gida ya kwana ba kuma girkin Umma ne sai tak'i toya k'osai ta dama zallar kunu kad'ai ta bawa Nimha 200 ta siyo musu iya su da Iya kawai, wannan dalilin ne yasa Mama ta yi musu jolof in taliya saboda kunu kad'ai bazai rik'e cikinsu ba kuma Nusrat ba ta shan kunu sai koko. Muryar Hidaya suka ji ta na k'wallowa Nusrat kira tab'e baki Shukhura ta yi bayan ta zuba taliyar a bakinta tace. "Ga su shafi da mai nan an faso. “ Wata muguwar harara Mama ta jefeta da shi, kawai sai tai murmushi ta sunkui da kai, daga bakin k'ofa Hidaya ta tsaya, ta tsuguna har k'asa ta gaisar da Mama kana ta dubi Nusrat da ke kallonta ta na murmushi, ta yafitota da hannu had'e da fad'in. "Kizo Yaa RJ ne ke kiranki, tsam Nusrat ta mik'e dama jikinta da hijabi saboda ba ta rabo da shi a jikinta ta bi bayan Hidaya suka fice Mama ta bita da idanuwa, Shukhura ce tace. "Nifa Mama sai nake ganin Aunty Maryam kamar ba ta son Yaa RJ ya na kula Yayarmu.“ "Rufe mini baki ko na dakar miki shi da hannuna, na fa gaya miki ba na son irin magan ganun nan ko? Idan ma ba ta son ya kulata naga ta dalilinta duk kuka sanshi.“ "Yi hak'uri Mama, amma kuma in saboda kar wata alak'a ta shiga tsakaninsu ne to ta sha kurumunta in Allah ya yarda mijin Yayarmu ba daga tsatson mijinta zai fito ba ehe. “ Girgiza kai kawai Mama ta yi don zuciya ta kusa ciyota ta k'wala mata mificin da ke kusa da ita, zama Shukhura ta gyara had'e da gyara murya tace. "Mamarmu nidai na gaji wallahi, ko yaushe sai ki dinga hanamu fad'a ana kuma k'wararmu, nidai wallahi idan Baba ya dawo zan kwashe duk abinda matarsa ke mana a gidan nan in gaya masa, haka kawai yanzu da ba dan muna da wannan taliyar ba sai dai fa mu zauna da yunwa har rana da ranar ma ba wani ishashh......“ Dakatawa ta yi da maganar sakamakon mificin da Mama ta rafka mata don taga hararar da take wurga mata ba za ta saka ta rufe mata baki ba sai ta had'a da duka, mik'ewa Shukhura ta yi ta na zunb'uro baki, ta figi hijabinta da ke kan k'ofa, ta na matsar k'wallar k'arya ta fice ta na. "Wallahi na kusa yin maganin wata a cikin gidan nan.“ Ta fad'a da k'arfi yadda Umma da ke d'aki za ta jiyo ta. Aunty Maryam na shiga d'aki ta tarar da Iya da kumburarran goshi. "A'a Iya me ya sameki haka?“ "Zamewa na yi na fad'i na buge da bango. “ "To wannan karcewar ta gefen fuskarki fa?“ "Ke nifa ba na son tambaya, na gaya miki zamewa na yi na fad'i, me kuma kike son ji, kin wani titsiyeni kamar wata uwata sai kinji abinda ya sameni sai kace wani abu za ki iya a kai, mtssss. “ Taja tsaki taci gaba da sababi yayin da Aunty Maryam tace. "Allah ya huci zuciyarki.“ Ta fice daga d'akin, in ba haka ba ba za ta daina sababin ba, ta shiga d'akin Umma don su gaisa. A cikin mota Nusrat ta samu Yaa RJ, tun fitowarta yake sakar mata murmushi ta cikin gilashin motar har ta k'araso gaban motar, a bud'e murfin motar yake don haka ta shiga ciki ta zauna suka had'a ido da Hidaya da ta juya ta koma cikin gidan. Shiru ne ya biyo baya sai kanta da ta sunkuyar k'asa ta na watsa da yatsan hannunta, yayin da shi kuma ya kafeta da idanuwansa, ya na jin wani sabon yanayi a kanta, ya san Nusrat yarinya ce ta yi k'ank'anta ya furta mata kalmar soyayya, amma ya na jin tsoron ya dawo ya tarar wani ya riga shi nasarar karb'ar soyayyarta, sanyin halinta, yanayin tafiyarta, yanayin maganarta komai ya yi dai-dai da yadda yake son matarsa ta kasance. "Ina wuni Yaaya?“ Nusrat ta katse shirun da yake tsakaninsu ta kuma katse shi daga tunanin da ya tafi, rintse idanunwansa ya yi ya busar da wata iska mai sanyi saboda yadda muryarta ta shiga jikinsa ta zauna, wani siririn zoben azurfa ya ciro daga d'an k'aramin yatsan hannunsa. "Muga hannunki. “ Zara zaran yatsunta ta mik'a masa ya zira mata a yatsanta na kusa da babban yatsa. "Daga nan kaduna zan wuce ta nan jirginmu zai tashi zuwa Uk nan da shekara uku zan kammala karatuna na dawo, ki mini alk'awari ba za ki bawa ko wani saurayi damar k'ulla soyayya da ke ba. “ Ba ta gane inda maganarsa ta dosa ba, don haka ta tsira masa idanuwanta kamar me karantar amsoshin tambayoyin da ke dank'are a zuciyarta, yayin da shi kuma yake jin kallon da take masa har tsakiyar zuciyarsa. 'Meye dalilin da yasa ka bani zobe, me yasa zan maka alk'awarin k'in kula ko wani saurayi bayan ba ni da tabbacin sona kake, idan ma sona kake anya auranmu zai yuhu kuwa, kana ganin Aunty Maryam za ta bar Katangar alak'ar da take ginanna a tsakaninsu taci gaba da ginuwa?' Wa'yannan tambayoyin sune cunkushe a ranta amman ta k'asa furta ko da kalma d'aya, ji take bakinta yai mata matuk'ar nauyi. Hannunta ya matsa had'e da fad'in. "Pls Nusrat. “ Tsintar kanta kawai ta yi da d'aga masa kanta, ya saki kyakkyawan murmushi, ya d'auko wata leda ya d'ora a kan cinyarta. "Na gode Nusrat, Allah ya baki ikon cika mini alk'awarina, bari ni zan wuce, ki gaida mini da su Mama. “ "Za su ji insha Allah, Allah ya kaika lafiya, ya kuma baka sa'a akan karatun naka.“ "Aminnnnn“ Yace yana me jin dad'in addu'arta yayin da ita kuma ta fice ba tare da ta d'au ledar da ya ajiye mata ba, murmushi ya yi don ya san za'a rina, a dai-dai lokacin Shukhura ta fito ta na zunb'uro baki, da hannu ya yafitota tazo gareshi, d'an risinawa ta yi ta gaisheshi yace. "Ga leda nan d'auki ki kaiwa Mama kice ina gaisheta.“ "Tom, an gode. “ Ta d'auki ledar shi kuma ya ja motarsa yai gaba. _RIDWAN JIBRIL shine cikakken sunansa yayin da ake masa inkiya da RJ, mahaifinsa da Yusuf mijin Aunty Maryam uwarsu d'aya ubansu d'aya, mahaifinsa ya rasu tun ya na yaro a gurin mahaifiyarsa yake da take aure a kaduna, tun bayan auran Yusuf da Aunty Marya ya d'auko RJ ya dawo gurinsa da zama suka rik'eshi tamkar d'ansu na cikinsu, bayan gama karatunsa na_ _secondary ya turasa Uk acan yake had'a karatunsa a fannin jarida._ _Hidaya da Nusrat tasu tazo d'aya sosai, suna k'aunar junansu hakanne yasa Nusrat take yawan zuwa hutu gidansu, yayin da shak'uwa me k'arfi ta shiga tsakaninta da Rj, har ta rikid'e ta koma soyayya a zuciyar RJ, idan har zaije kaduna gurin mahaifiyarsa sai ya fara tsayawa gurin Nusrat ya yin da k'arara Aunty Maryam ke nuna ba ta son alak'arsa da Nusrat saboda akwai wani buri da suka ci a kansa ita da mai gidanta._ Kwata² Shukhura tak'i yadda ta shiga ko gurinsu, ta na filin babban tsakar gida a zaune ta na dakon zaman jiran Baba ya dawo, don kada ma Mama ta hanata aikata abinda tai niya, ledar da RJ ma ya bata a bakin k'ofar d'aki ta ajiye ta fito don duk kada Mama ta ruguza mata shirinta, ta san dai duk tsiya Baba bazai wuce 12 na rana bai dawo ba saboda ba a gida ya kwana ba. Har kusan k'arfe d'aya Baba bai shigo cikin gidan ba, har ta fara tunanin tashi ta jiyo takun tafiya don haka ta maida idanuwanta kan k'ofar shigowar, aikuwa Baban ne ya yi sallamar ta amsa masa ta nufeshi had'e da d'ora damuwa akan fuskarta, har da fara taro k'walla, gaban Baba ne ya yanke ya fad'i yace. "Lafiya Shukhura me ya faru? “ "Baba.“ "Na'am fad'a mini me ya faru? “ "Dama kullum Mama ce ke hanani gaya maka.“ "Ina jinki.“ "Duk ranar girkin Umma ba ta bamu abinci ishashshe, da kai da Iya da su ta ciccika muku kwano, kuma har d'anye take ragewa ta b'oye, to yau da safe ba ta toya mana k'osai ba zallar kunu kawai ta dama, ta bawa Nimha ta sayo musu su da Iya. “ Ran Babane ya yi mugun b'aci, ya tabbata Shukhura ba za tai masa k'arya ba, shafa kanta ya yi yace. "Jeki ciki zanwa tufkar hanci. “ Cike da murna ta shige ciki ta na jin kamar ta sauke abu me nauyi a zuciyarta ko kad'an ba ta damu da hararar da Mama ke ta zabga mata ba. Sai da ya bari Umma ta gama girki ta raba kowa ta kai masa shima ta kawo masa nasa sannan ya k'wallowa Shukhura kira, ta amsa ta fito da saurinta. "D'auko mini abincinku.“ "Toh." Tace da hanzari ta juya ta d'auko. "Jeki ki anso mini na Iya. “ "Ai yau Iya ba ita kad'ai bace su Aunty Maryam sun zo. “ "Af na sha'afa, da na shiga gurin Iyanma mun gaisa, bar na tan. “ Ya dubi Umma yace "D'auko mun naku, kuma bance ki rage komai ba, inma kin rage da kaina zanzo na duba.“ Tsuru² Umma ta yi da ganinta ka san ba ta gaskiya taje ta d'auko ta kawo masa duban Shukhura ya yi yace. "Je ki d'aki, ki turo mini Mamanku. “ Shukhura na barin gurin Baba ya dubi Umma yace. "Yanzu wannan adalci kenan? Kalli abincin da rai d'aya zai ci, ki dubi na rai biyu duk sun taka wanda rai hud'u zai ci kinwa kanki adalci? Ko iya Nimha kad'ai ai sai ta tashi da wannan abincin, idan ni ba na gani ai Allah ya na ganinki kuma hakk'insu bazai tab'a barinki ba. “ Fad'a sosai Baba ya shiga yiwa Umma kamar zai ari baki, ya shaida mata muddun ta kuma irin rabon nan to sai ta bar masa gidansa, Mama da tazo fad'an ya rufe ta da shi akan me za ta hana a gaya masa irin haka na faruwa a cikin gidansa ya d'au mataki tunda ita ba ta gaya masa ba, ita dai Mama hak'uri ta bashi don sosai Baba ransa ya b'aci, ranar huni ya yi ya na surfawa Umma fad'a, abincinma ya yi zuciya ya k'i ci ya juyewa su Shukhura akan nasu na su Umman ma ya datsi rabi ya k'ara musu akai ya kira Shukhura ta d'auka, Umma kuwa sai huci take kamar ta janyo Shukhura tai ta jibgarta. _____________ Bayan sati guda Baffa Shamsu yazo garin zariya, a lokacin su Aunty Maryam sun koma kwana uku sukai suka tafi. Transfer yake nema zai dawo zariya gaba d'aya hakanne yasa yazo don neman gidan da zasu samu su zauna, duk da nan kusa da gidansu an masa tallansa to dai ya na son siya amman dai ba su gama cininki ba, tun zuwansa Iya tace. "Nidai yau aradu shinkafar gwamnati zanci, don wallahi na gaji da cin shinkafar hausa ina karo da tsakuwa ta na farfasa mini hak'ori, kalli nan kaga yadda duk hak'orina ya farfashe, don haka ma ni wallahi in za ka tafi binka zan, don na gaji da cin tuwon masara kullum da daddare na kwanta, gara a dinga dafa mini taliyar nan ta gwamnati me dad'in gaske.“ Murmushi kawai Baffa Shamsu ya yi yace. "Haba Iya ba na son kina irin wa'yan nan magan ganun kema dai kinsan Yaya yana matuk'ar k'ok'ari, idan yaji abinda kike cewa bazai tab'a jin dad'i ba.“ "To kar ya ji dad'in mana ni ina ruwana, wani k'ok'ari yake banda son 'yarsa da ya fifita a kaina. “ Ko me ta tuna kuma sai tai shiru kana tace. "Mubar ma maganar d'an arzik'i maza je ka siyo mana shinkafar, ka kuma siyo mana kaji don yau mu d'an wasa bakinmu, don rabona da ci nikam ina jin tun kan rasuwar Malam. “ Girgiza kai kawai Baffa Shamsu ya yi ya na mamakin halin mahaifiyar tasu sam ba ta da godiyar Ubangiji, duk zuwan da zaiyi sai sunci kaji a gidan, haka zalika Baba ma idan ya ji aljihunsa da nauyi ya na siyo musu su ci amma wai kunji rabonta da ci tun kan rasuwar Malam. Buhun shinkafa biyu da katan na taliya da macaroni biyu Baffa Shamsu ya siyo musu ya ajiye su a d'akin Mama, ya siyo musu kaji guda biyar manya ² gashi kuma aka taki sa'a girkin Umma ne, don haka Shukhura ta na da 1000 tace bari taje titi ta siyo don ta san 'yar kad'an za'a sanmusu, Nusrat ma na da 1000 sai ta bata ta siyo musu guda biyu kuma manya da su. Ilai kuwa cinya d'aya fukafiki aya sai wuya aya aka saka musu, ko kad'an ba su damu ba Shukhura ta wanke nasu ta tafasa ta fara suya. K'amshin suyar naman Iya ta ji a ranta tace kaddai matar nan ragewa ta yi take soyawa da hanzari ta fito don ta ganewa idonta, ganin Shukhura ce me suyar ta kai hannu za ta d'auka a cikin wa'yanda ta kwashe, Shukhura ta yi saurin d'auke robar hannun Iya ya sauka a k'asa har sai da ya yi k'ara tace. "Auchhhhh“ Don ta ji zafi sosai, Shukhura kuwa ko a jikinta ta murgud'a baki tace. "Ai ba taku bace, wannan tamu ce naje na siyo, da za ki d'auko yamutsats tsan hannunki ki saka mini a ro....“ Ba ta k'arasa ba taji saukar mari a kuncinta, dafe kuncin ta yi ta tsaya ta na kallon Mama da ta fusge robar naman a hannunta ta d'auki cinya manya² guda biyu ta bawa Iyan, sai da Iyan ta ansa kana ta tab'e baki. "Ai da ba ki daketa ba ai na san duk makirci ne irin naki, ke kitsa mata dukkan abinda takeyi a gidan nan, amma ai Shamsu yazo zai mini maganinta. “ Ta na kawowa nan ta fice daga gurin Shukhura ta bita da d'an iskan kallo, Mama ba ta iya cewa komai ba ta koma d'aki Shukhura ta k'wallowa Nusrat kira. "Yayarmu zo ki kama mini na shiga band'aki. “ Nimha tace. "Kawo na miki kan ki dawo. “ "Don aji dad'in d'iba akai d'aki ba, a'a basshi na gode ga Yayarmu nan za ta ansa. “ Umma ta gallawa Nimha harara. "Maganin shishshiginki kenan ga shinan an gab'a miki magana.“ Memakon Shukhura ta shiga band'aki sai ta fice ta yi gurin Iya. "Kina ina yau in kinci naman nan ba Mama ce ta kawoni Duniya ba. “ Iya na jin haka ta yi saurin nad'e shi a leda ta saka a k'ark'ashin gado, dama ajiyeshi ta yi sai ta gama da na cikin miyar. A bakin k'ofa ta cage tace. "Ki fitomun da namana.“ Sai ki d'auka in kin ganshi ai. “ Bin d'akin tai da ido ta na nazarin inda Iyan za ta ajiye naman, ganin kamar idon Shukhuran ya na sauka a k'ark'ashin gado Iya ta yi saurin d'aukewa ta mik'e tsaye. "Sai kizo ki k'wata in baki da kunya. “ Kanta Shukhura ta yi gadan² ta kama hannunta za ta murd'e. "Ke ke ba ki da hankali wai. “ "Eh bani da shi d'in, ta d'auka ta baki naman sannan ki yab'a mata magana kuma kici alqur'an ba ki isa ba. “ Taci gaba da k'ok'arin k'watar naman dai-dai nan Baffa Shamsu ya shigo. Kyakkyawan maruka ya saukewa Shukhura kana ya tambayi ba'asi Iya ta koro masa bayani, hararar Shukhura ya yi da ke tsugune dafe da kuncinta. "Dama ance ba ki da kunya to yau zanyi maganin rashin kunyarki. “ Ya zari cagar radio ya yo kanta ta saki ihu ta yi bayan Iya dai- dai lokacin ya kawo mata duka ya sauka a jikin Iya, Iya ta zunduma ihu tsabar azaba. "Shamsu ka rabu da yarinyar nan dan Allah kar ka daketa, bai saurari Iya ba ya b'anb'aro Shukhura daga jikinta ya hau zuba mata wayar ko ta ina, aikwa ta bud'e murya ta dinga zunduma ihu, Mama ko motsi daga inda take ba tai ba, kuma ta hana su Nusrat zuwa, tace ai gara taji a jikinta gobe ma ba za ta sake ba, Umma kuwa da gudu ta nufo gurin ta na shewa dama a ciki take da ita. Sai da ya yi mata lilis sannan ya k'aleta,ya fice, Iya na gefe ta na ta matsar k'walla don ta san yau kashinta ya bushe gurin Shukhura, yayin da Umma ke ta shewa ta na fad'ar magan ganu. "Yau dai an mana maganin mara kunyar gidan nan, aiyiri yiri yiri yiri. “ Wani kukan kura Shukhura ta yi ta saki wani ihu ta yo kan Umma da gudu, tsoro ne ya kama Umma ta mik'e za ta fice ta yi tuntub'e ta fad'i, yayin da Shukhura ta shiga aljanun k'arya ta dinga cin uban Iya da Umma da sanda dukkanninsu sun jigata sosai, har sai da Mama tazo ta janyeta, suna shiga d'aki ta fashe da dariya a ranta tace. 'Saura Baffa Sham sun.' Mama kuwa zuba mata ido kawai ta yi, don ta d'auki alk'awarin ta daina dukanta daga yau, addu'ar nan ita za ta cigaba da yi mata anai mata rubutu ta na sha. Da jan jiki Umma ta samu ta komo gurinta, ta na jin mugun shakkar Shukhura a ranta, Iya kuwa kuka ta dinga rusawa don yau babu abinda zaisa ta kwana a cikin gidan nan Shamsu yazo su tafi Kaduna ta wuta da wannan jaraba da masifar da Audu ya haifa. Hankalin Shukhura bai kwanta ba har sai da ta sakawa Baffa Shamsu cinnaku biyar manya² a riga ai kuwa ya sha muguwar azabar da ta wuce dukan da yai mata. 300 za ku biya domin samunsa cikin sauk'i. NABABA FADILA SHU'AIB GTBANK In kuma katin wayane ku turo ta wannan layin, shaidarki ta biya ma ki turo cikinta. 09037093702 In katin wayane 400 zaku biya. Garab'asa gareku masoyana duk wacce ta sayi wannan littafin za ta sami wanda zan rubuta gaba kyauta, ban yadda ki sayi littafina ki dinga turawa gruop ba, in hakan za kiyi ki sameni a layina muyi magana. Allah ka k'arawa mahaifanmu lafiya da nisan kwana, Amin. #Team KTG #N.W.A [10/8, 3:42 PM] Binta Lawan: *BEBE'ARTH* Wattpad@Rashuna *KATANGA* ____________ *SIX* Ta b'angaren Alhj Faruoq Fanda kuwa ya na zuwa gida ya sanar da matarsa Hajiya Suwaiba wata yarinya ta yi wuff da zuciyar yaronsu, farin ciki tsanta H.Suwaiba ta shiga had'e da fad'in "Wata yarinya ce wannan mai matuk'ar sa'a Alhaji?“ "Ai ban baro gurin saukar nan ba sai da na saka aka samo mini bayanai a kanta. A nan unguwar cikaji suke zaune, mahaifinta ba wani mai hali bane sai dai rufin asiri na Ubangiji, itace 'ya ta biyu a gurinsa, ta na matakin aji biyu a sss, an shaidu 'yan gidan gaba d'ayansu da tsantsar tarbiya, sunanta na gaskiya Safiyya, amma da Shukhura ake kiranta.“ K'awataccen murmushi H.Suwaiba ta saki tace. "Kai amman na ji dad'i, Allah yasa itace abokiyar arzik'insa, ai banda hidimar saukar nan da muke ta Maryam da ba abinda zai saka ni zuwa naga sirikata a yau.“ Murmushi Alhj ya yi yace. "Don zumud'i irin naki, gobe in sha Allah dai zamu je gaisuwa, da kayan na gani ina so, don har ga Allah na yaba da zab'in yaron nawa, don dama ina gudun ya d'auko mana irin wayayyin yaran nan marasa tarbiya, fatanmu dai Allah yasa ba maganar wani a kanta.“ "Amin., amma ka dai sanar da Hajiya Inna ko, don gara a gaya mata tun wuri za'a yo mata kishiya. “ Ta kai k'arshen maganar ta na dariya, dariyar shima Alhajin ya yi yace. "Ita ai na fara gayowa ta na nan ta cika fam ta na jiran shigowarsa, na san yau dai ba za'a bashi abinci ba nan za'a koro mana shi. “ Alhj Farouq Fanda asalinsa d'an garin Fanda ne, neman kud'i mahaifinsa yazo yi tun Farouq na yaro, a garin kano suka fara zama ya na yin kasuwancinsa kuma Allah yasa masa albarka a ciki, nan da nan ya tara dukiya me d'imbin yawa, Farouq shi kad'ai ne d'ansa wannan dalilin ne yasa ya bashi gata mai yawa, ranar da Faruoq ya gama karatunsa na shari'ah a ranar mahaifinsa ya rasu, sunyi kuka iya kuka da shi da mahaifiyarsa Fatima (Hajiya Inna. ) Bayan rasuwar mahaifinsa ne dukiyoyinsa duk suka dawo k'ark'ashinsa, sannan kuma ya fara aiki a matsayinsa na babban alqali, nan da nan dukiyarsa ta kuma bunk'asa, ga kuma harkokin kasuwancin mahaifinsa hakan ne yasa ya nemi mataimaka kuma ya samu masu aminci, daga kano suka tarkata suka koma zariya da zama a unguwar sabon gari, gida ya dank'ara ba na wasa ba, ya yiwa Hajiya Inna sashinta da ban, zuwansa zariya anan ya had'u da Hajiya Suwaiba suka fara soyayya itama 'yar garin zariyan ce anan unguwar cikaji, ba'a d'au wani lokaci ba akai bikinsa da Suwaiba, Hajiya Inna na mutuk'ar k'aunar sirikar tata, ko kad'an ba ta san wani mugun hali na uwar miji da ake fad'a ba, ta rik'eta tamkar 'yar cikinta, wannan dalilin ne yasa tai alqawarin idan Allah ya azurtata da 'ya'ya maza za ta k'aunaci matansu kamar 'ya'yan cikinta, don a ganinta babu bambamci tsakanin d'anka da sirikar taka tunda an riga an zama d'aya. 'Ya'ya biyu Allah ya azurtasu da su, Mustafa,sai Maryam, sunga gata sosai gurin mahaifan nasu. Mustafa Faruoq Fanda, wanda abokansa ke kiransa da Fanda ya kammala karatunsa na low har ya zama Barrister mai zaman kansa, komai na shi na rayuwa a sashin Hajiya Inna yake don ta na matuk'ar k'aunarsa, Maryam kuwa rayuwarta ta fi k'arfi a gidan kakanninta na uwa acan cikaji, da yake suma da rufin asirinsu, zamanta a cikaji shiyasa islamiyarsu tazo d'aya da su Shukhura, ba ajinsu d'aya ba, da yake aji biyu ne aka had'e akai saukar, itama Maryam ta yi candy ta na jiran sakamako don ta d'ora daga inda ta tsaya. Wannan kenan. Washe gari da safe Iya ta sami Mama a lokacin ta na toya k'osan da zasui kari da shi tace. "Waini Maimuna ba'a kasafta kud'in nan bane? Na ji shiru ba'a ce Iya ga naki ba. “ "Wani kud'i?“ Mama ta tambayeta don ita a tunaninta wasu kud'i ne Baba ya samu da ban. "Ban gane wani kud'i ba, ki jiki da wata iriyar tambaya, to kud'in da jikokina suka samo.“ D'an k'aramin murmushi Mama ta yi tace. "To ki bari in Babansu ya tashi sai ki tambayesa, in kuma in taso miki shi to? “ "Aini na san ba za ki bari a bani ko ficika a kud'in nan ba Maimuna, na rasa me na yi miki a duniyar nan kika bi kika tsaneni daga ke har 'ya'yanki bare ma waccan me tak'adiriyar k'irar samudawa, da fari kamar arnan zabiya, na tabbata da Nimha ce ta samo kud'in nan biyu za'a raba a bani, amman da yake ku mugaye ne an halicci rowa a jininku biyar kun gagara ba ni, kuje kui ta ci insha Allahu sai kun shekara kuna zabga gudawar da ba ta da comlayin, tuban sardauna kawai.“ Shukhura da Nusrat da ke kallo a 'yar k'aramar wayar Mama, duk suna jin abinda Iya ke cewa, zumbur Shukhura ta mik'e ta fito. "Ki gani a kanki me mugun alkaba'i, insha Allahu kanki bakinki zai komo, naga kud'i namu ne ko, to ba za'a bayar d'in ba kiyi abinda za ki, rowa kuwa mu muka yanke mata cibi, kuma zan nuna miki ni babbar tak'adirya ce don naga kwana biyu kin manta da tak'adirancin nawa, inma tuban galadima ne ko wambai tunda mu musulmai ne Alhmdlillh. “ Tun fara maganar Shukhura Baba ya fito, shi yaiwa Mama alamar ta yi shiru daga k'ok'arin dakatar da Shukhura da take har sai da Shukhuran ta kai aya ya ja hannun Iya suka fice da ke neman fisgewa ta na d'an kuka, sai da sukaje d'akinta sannan ya sake ta yai k'asa da muryarsa sosai yace. " Tun da na auro Maimuna gidan nan take d'aukar cin kashinki Iya, ba ta tab'ai miki kallon banza bare musu da ke, amman har ta haihu kina yi a gaban 'ya'yanta wanda Shukhura ba ta iya d'auka har sai ta rama sannan kuma kisa in daketa k'arshe kuma kanki abin zai dawo, amman har yau kink'i daina abubuwan da kike, maganar kud'i kuma da kike yaran nan daga su har mahaifiyarsu biyar basu karb'a ba ni suka barwa saboda hidimar gida da kuma auransu in ya taso amman kuma kinzo kina fad'ar maganganu a kai, yanzu meye ribar sa'insa da jikarki? Dan Allah Iya ki canja, ki dinga jan girmanki.“ Kuka iya ta ja had'e da fad'in. "Tashi ka fita Audu, tashi ka fita nace tun kafin na tsine maka ka bi duniya, har ni za kazo ka gayawa maganganun banza, a gabanka 'yarka tai mini cin mutumci ka kasa d'aukar mataki saboda an baka kud'i? Jeka kawai Audu na barwa Maimuna da 'ya'yanta kai.“ "Kiyi hak'uri Iya, yanzu zanje na lillisa mata jikinta. “ Kukan Inna ne ya tsaya cak tace. "Idan har kana son albarka a gurina kada ka tab'a lafiyar tak'adiriyar yarinyar nan, don wallahi kaf tak'adirancinta za ta sauke mini yau.“ B'oyayyen murmushi Baba ya yi ya tashi ya fita. Yusra da ta dawo daga siyo sikarin da Mama ta aiketa tacewa Mama. "Wasu a mota sunce suna sallama da Baba. “ Baba da shigowarsa kenan maganar ta sauka a kunnensa ya juya had'e da fad'in. "Bari naje naga su waye.“ Sai kuma gashi ya dawo yace Yusra ta d'auko tabarmi, ta d'auko taje ta shimfid'a a soro. Bayan gaishe² Alhj Faruoq ya gabatarwa da Baba abinda ke tafe da su, sannan ya d'ora da cewar. "Da fatan ba maganar wani a kanta. “ Baba yace. "Ba maganar kowa a kanta, kuma na yi masa izini yazo ya nemi soyayyarta idan har ta amince mishi babu abinda zai hana na bashi ita, Allah ya tabbatar mana da alkhairi. “ Godiya Alhj Faruoq sukai da shi da abokinsa da suka zo tare, sannan ya sanya driver d'insa da ya tuk'osa ya fito da akwatin da suka zo da shi, akwati ne mai kyau madai daici, Alhj Farouq yace. "A bawa Shukhura, kayan sun gani suna so ne. “ Baba yace bazai karb'a ba suka ce ai 'yarsu suka kawo, idan kwa bai ansa ba to baiyi na'am da su ba, daga haka sukai masa sallama suka tafi shi kuma ya ja akwatin ya nufi cikin gida...... 300 za ku biya domin samunsa cikin sauk'i. NABABA FADILA SHU'AIB GTBANK In kuma katin wayane ku turo ta wannan layin, shaidarki ta biya ma ki turo cikinta. 09037093702 In katin wayane 400 zaku biya. Garab'asa gareku masoyana duk wacce ta sayi wannan littafin za ta sami wanda zan rubuta gaba kyauta, ban yadda ki sayi littafina ki dinga turawa gruop ba, in hakan za kiyi ki sameni a layina muyi magana. Allah ka k'arawa mahaifanmu lafiya da nisan kwana, Amin. #Team KTG #N.W.A [10/8, 3:42 PM] Binta Lawan: *BEBE'ARTH* Wattpad@Rashuna *KATANGA* ____________ *FIVE* A haka rayuwa take juyawa cikin d'an k'aramin familyn nan, Nusrat ta yi candy, su Shukhura kuma saura shekara d'aya su yi, a lokacin ne kuma aka saka musu ranar saukarsu ta islamiya da yake duk ajinsu d'aya har Nimha. 3/4/2014 shine ya kama ranar saukar tasu. Iya ba ta sauya daga halinta na nuna banbanci tsakanin jikokinta ba har ma ga 'ya'yan nata, don yanzu Baba bai samun cininki sosai a kasuwa sai ya zamto abinci ma Baffa Shamsu ne ke ajiye musu duk wata, saboda ya dawo nan kusa da gidan nasu da zama. Hakan da matarsa ta gani ne yasa ta d'au babban mataki a kansa, abincin da yake sauke musu sai ya koma saukewa gidan su matar tasa duk wata, gaba d'aya ta bi ta mallake shi ta kanainaye shi ba ta bari ya morawa kowa abin biyar face 'yan uwanta, zagi da tsinuwa kuwa ta na shan shi gurin Iya amma a bayan idonta, in a gaban idonta ne kanzil ba ta iya tofawa, saboda abincin da take kawo mata rana da dare kar taje a daina kawo mata ta shiga uku da cin tuwo don yanzu sai su jera sati suna cinsa huni sir, don yanzu rayuwar gidan lallab'ata suke duk abinda Baba ya samo ciki ake k'ok'arin bawa hak'k'insa. 3/4/2014 Ta kama ranar lahadi kenan, ranar da zuk'ata da yawa ke cikin farin cikin kammala saukar karatun alqurani mai girma, za'a bawa kowa allonta na shaidar saukarta, irin wannan ranar ce ko wani bawa ke burin ta riskesa. Tun daga farkon layin makarantar tasu mak'il yake da mutane ko 'yan saukarma ba'a hangowa saboda suna tsakiya a cikin rumfa,banda sautin qira'ar Shukhura mai matuk'ar dad'i babu abinda kake juyowa a gurin mutane da dama sun nutsu suna saurarar karatun da ke saukar da nutsuwa a zuk'ata. Bayan kammala karatun Shukhura ta taso a hankula ta koma gurin zamansu, tun tasowarta FANDA ke binta da kallo, duk da kasancewar ga tsantsar yarinta nan a fuskarta ya na kallo amman kuma ta kama zuciyarsa sosai, tabbas idan ya bari lokaci ya shud'a wani ne zai riga shi mallakarta, don irin su Shukhura ba wanda ake kalla a kau da kai bane, bare nan gaba ta k'ara girma, har ta zauna idonsa ya na kanta, a hankali ya sauke idonsa akan wacce ke Kusa da ita, tabbas ya gano kama a tattare da su ya na kyauta zatan 'yan biyu ne, duk kallon da yake binta da shi mahai finsa Farouq Fanda na lura da shi, ko ma wacce yarinyace wannan tabbas ta taki sa'a gurin d'an nasa, kallo d'aya idan yaiwa mace to tabbas ta taki babbar sa'a, tun kammala karatunsa yake masa zancen aure amma yake tai masa kwana kwane, amman yau yaga alamun d'an nasa yayi kamu, idan kuwa hakane zai fi kowa farin ciki, bare kuma mahaifiyarsa ta ji labari da Hajiya Inna, murmushi ya yi ya na gano yadda Inna za ta d'auki zancen. Kallonsa ya yi har lokacin idonsa na kan Shukhura, wani kyakkyawan murmushi ya saki ya saka bakinsa dai² kunnansa yace. "Da dukkan alamu dai yau yarona yaga matar aure. “ Kunya ce tai mugun kama shi, ashe dai duk abinda yake mahaifinsa na lura da shi, shafa kansa ya yi ya na mai sunkui da kai, shafa kansa Abban nasa ya yi yace. "Soyayya ta na da kyau yarona, Allah yasa matar arzik'i ce. “ A can k'asan mak'oshi ya amsa da "Amin“ Ya na mai jin muguwar soyayyarta a zuciya wannan shi ake kira love at first sight. Bayan kammala saukar aka fara kiran d'aliban da sukai na d'aya zuwa na goma don a basu kyauta. Aysha Abdullahi Ahmad aka fara kira wacce tai na d'aya sannan aka kira Safiyya Abdullahi Ahmad ita tai ta biyu sai Maryam Farouq Fanda da tai na uku daga haka har aka kai na goma duk aka basu Kyaututtukansu, anan Alhaji Faruoq Fanda ya karb'i speaker yai magana akan ya bawa makaranta kyautar million d'aya, sannan ya bawa Aysha Abdullahi Ahmad da Safiyya Abdullahi Ahmad kyautar million d'aya, saboda yaba k'wazonsu, cikin d'alibai kusan 100 su suka d'au matakin na d'aya da na biyu. Nan gurin taro ya hautsine kowa na fad'in albarkacin bakinsa, yayin da wasu ke cewa ai kyautar million biyu gurin Alhaji Farouq Fanda ba komi bace kamar biyar haka yake jin ya cire daga aljihunsa. Iya kuwa sai dashe baki take ta na kuma b'antarar goronta, ta kalli Umma da ranta yai bak'ik'k'irin saboda bak'in cikin Shukhura da Nusrat, harara Iya ta galla mata tace. "An dai yi asarar haihuwa, ace duk kyaututtukan nan da ake rabawa babu sunan Nimha ko d'aya, saboda k'wak'walwarta irin ta jaki ce, amma kalli 'ya'yan albarka, gaskiya Maimuna ta iya haihuwa banda kyaututtukan da suka samo har kyautan million d'aya suka samo mana saboda 'yan arzik'i ne su irin albarka, don ni har ma na fara kasafta nawa kason da za'a bani, na san dai zan samu kamar dubu d'ari biyu, kinga dubu d'ari zan sayi kayan abinci har da su maltina da madara da su k'wai, da taliyar nan me kanannad'ewa ta gwamnati, d'aya dubu d'arin kuma na ajiye a hankula ina zara ina siyo gasashiyar kaza da youghot ina ci da daddare in tayar da kai, wayyo ai a cikin satin nan ma sai an k'asa gane ni zan canja kala saboda cin dad'i, fatar nan tawa da ta fara yamutsewa saboda wahala za ta gyaru, kai Allah dai ya shiwa Maimuna albarka da ta haifo wa'yannan 'yan albarkar, tun da nake ban tab'a rik'e dubu goma ta kaina ba, amman gashi dalilinsu zan rik'e,har dubu d'ari biyi, ni ban san ma tun tuni me ya hanani nuna musu k'auna ba wallahi, amman duk cikin jikokina Allah na gani na fi son su.“ Duk zubar nan da take ita kad'ai take yinta, don Umma ta bar gurin saukar tun sanda ta fara maganar, saboda ganin za ta d'ora mata wani bak'in cikin ne kawai, da ta jujjuya ba taga Umman ba itama sai ta nufo gida ta na tafe ta na kuma kasafta dubu d'ari biyun da za'a bata. Sai kusan k'arfe uku suka baro gurin saukar, saboda an yiyyi hotuna acan, a matuk'ar gajiye dukkaninsu suke, don haka ko waccensu sai da tai wanka kafin su kwanta zuwan jiran yamma ta yi, duk da gidan nasu a cike yake da 'yan hidimar saukar. Da yamma sukai walimarsu anan cikin gidan, kaya iri d'aya suka saka dukansu, Aunty Maryam ce ta d'inka musu, itace ma ta d'au nauyin kayan snacks d'in da suka raba a walimar. Har kusan dare Iya na d'akin Mama tak'i tafiya sai jan Mama take da hira, Mama kwa sai dai tai ta binta da um da umum saboda rashin sabo. "Aini fa ko, tun tuni dama ina sonki da 'ya'yanki dama duk makircin shegiyar matar can ne wallahi, kullum ita kenan kawo mini b'atanci akanku, ai gashinan ta haifi yarinya mai k'wak'walwa irin ta jaki, da k'afafuwanta kamar na babyn roba. “ "Uhm“ Mama tace kawai, ta na mik'ewa don jin ana kiran sallar isha, in ba sallar ta tayar ba Iya ba za ta k'yaleta da wa'yannan zantuttukan nata mara sa kan gado ba, ganin Maman ta tayar da sallah yasa Iya ta tashi ta fice ta na jifan d'akin Umma da banzan kallo, Umma ta na hangota ta labule a ranta tace. 'Makirar mata kawai, insha Allahu k'wandala ba za'a baki cikin kud'in ba inga ta tsiya, ina nan kuma za ki dawo jikina in miki rashin mutumcin da har ki koma ga mahaliccinki baza ki manta shi ba, tsohuwar banza kawai.' Iya tun ta na jiran shigowar Baba yazo a kasafta kud'in, har bacci yai gaba da ita ba tare da ta sani ba, Baba kuwa sai gurin 11 na dare ya shigo, bayan ya rufe gurinsu ya kirawo Mama da su Shukhura anan ya ke gaya musu. "Na kai Accaunt number d'ina makarantarku, Alhmdlillh d'azu na ji kud'inku sun shigo har million d'aya, yanzu me kuke gani za'ai da kud'in?“ Shiru dukkaninsu sukai su na kallon Mama, ganin Maman ba za tai magana ba yasa Nusrat tace. "Nidai Baba a shawarata kawai ka bar kud'in a Accaunt d'inka, in yaso sai a 'yebi wasu daga ciki a siyo kayan abinci, duk wata lalaura da za ta taso sai a magance da kud'in ko kuwa? “ Ta fad'a ta na kallon Shukhura. "Eh Yayarmu, nima hakan nake shirin fad'a kika riga ni. “ Murmushi Mama ta yi, ta na mai yabawa da hankalin yaran nata, kuma taji dad'in abinda suka ce da mahaifin nasu tace. "Na ji dad'i matuk'a da abinda kuka yanke, dama nak'i maganane don na ji ta bakinku, ku tashi maza kuje d'aki, Allah ya yi muku albarka. “ "Amin.“Suka amsa a tare suka tashi suka fita, bayan fitar tasu Mama ta kalli Baba tace. "Ta bakin nasu nima zanyi, ka d'ebi wasu kud'in ka siyo mana kayan abinci, kabar ragowar a asu sun naka, in yaso duk abinda aka d'an samu sai ka dinga ajiye su, saboda kwanan nan za ka ji auran yaran nan ya tashi, kuma duk su ukun nake magana, don Nimha da Shukhura sun fi Yayartasu gab'b'an girma, in suka jero sai ka rantse itace k'aramar su, shiyasa ma ita Yayartasu d'in ba saurayin da ke zuwa gurinta, sab'anin Nimha da Shukhura, bare ma Shukhura babu ranar banza da ba za'a zo ace ana sallama da ita ba, sai na tursasa ta take fita, sai tace ai wai ita Yayarsu ba ta zance. “ "Da gaskiyarki Maimuna, nima ina tunani idan akace mini auran yaran nan ya taso, duk dai da Allah na dogara shi na mik'awa lamurana, tabbas kuma da ace Nusrat na da tsayayye a yanzu zan aurar da ita, tunda ta yi candy tai sauka me kuma za'a jira, amnan tunda babu sai muyi rok'on Allah ya kawo mata na gari, su Shukhura kuwa babu zancen ai yayarsu ba ta zance, shi aure ai lokaci ne ba'a jiran sai yaya tayi sannan k'anwa za tayi, duk wacce ta samu miji zan aurar da ita, fatana dai Allah duk ya had'a su da mazaje na gari, kuma na ji dad'in shawararki hakan kuma za'ai Allah ya shiga lamarinmu ya kuma dafa mana. “ Mama ta amsa masa da. "Amin. “ 300 za ku biya domin samunsa cikin sauk'i. NABABA FADILA SHU'AIB GTBANK In kuma katin wayane ku turo ta wannan layin, shaidarki ta biya ma ki turo cikinta. 09037093702 In katin wayane 400 zaku biya. Garab'asa gareku masoyana duk wacce ta sayi wannan littafin za ta sami wanda zan rubuta gaba kyauta, ban yadda ki sayi littafina ki dinga turawa gruop ba, in hakan za kiyi ki sameni a layina muyi magana. Allah ka k'arawa mahaifanmu lafiya da nisan kwana, Amin. #Team KTG #N.W.A [10/8, 3:42 PM] Binta Lawan: *BEBE'ARTH* Wattpad@Rashuna https://my.w.tt/Cjpv9nxoJ9?utm_ *KATANGA* ____________ *EIGHT* Tun kan ta k'arasa soro k'irjinta ke dukan uku² shikuwa Mustapha alamun tafiyar da ya jiyo ne yasa shi k'urawa k'ofar da za ta fito ido, sai da ta janyo mayafinta ta rufe fuskarta kafin ta tako a hankali zuwa gurin da akai masa shimfid'a da tabarma zuciyarta na harbawa da gudun gaske, can gefe da shi ta samu ta zauna ta sunkui da kanta k'asa kafin tace. "Ina wuni.?“ "Nima ban ganshi ba, tun da dai ba ajiyarsa kika bani ba, idan kwa kina son na amsa miki to ki tabbata kin yaye rufin da ya Katange mini kyakkyawar fuskar da nake da muradin kallo a ko da yaushe. “ K'asa ta kuma yi da kanta ta na murmushi. "Please nidai a taimaka mini, yau kusan sati guda rabon da na ganta, tun a ranar da ta samu babban guri a zuciyata, idanuwana suka aminta da ita, suka tabbatar da itace sanyinsu kuma haskensu.“ "To aini kunya nake ji." Ta fad'a kamar a shagwab'e. "Idan kika sShukhuraki cikin nawa za ki daina jin kunyar. “ 'Cif, na ma kasa bud'e mayafina na ganshi, duk da zuciyata da take ta azalzalata na gansa shine har zan saka idona cikin na, hod'ijam aikam dai sai dai kar na daina jin kunyar' Muryarsa ce ta dawo da ita daga d'an k'aramin guntun maganar zucin da ta tafi. "Zan fa zo da kaina na cire mayafin gaba d'aya wallahi idan har ba ki d'aga sa ba.“ 'Cif saboda kai d'an ikka ne haka kawai ka ciren mayafina, hod'ijam aikam dai da kaga tsigalewa.' K'irjinta ne ya buga, zuciyarta tai wani irin harbawa yayin da ta jisa ya matso dab da ita. 'Laa kaddai ciren mayafin zaiyi kuwa, na shige yau na had'u da mara kunyar mutum.' Da sauri ta yaye mayafin da ke fuskarta, wani kyakkyawan murmushi Mustapha ya saki da yayi sanadiyar motsawar zuciyar Shukhura, wani fitinannen kyahu ta gani a tattare da Mustaphan wanda ba za ta iya bayyana muku shi ba saboda tsabar rud'ewa da cikar kyahunsa. Gira d'aya ya d'age mata had'e da fad'in. "Na miki ne? “ Lumshe idanuwanta ta yi don jin bak'on yanayin da ke sauka a ilahirin jikinta, ta d'au tsayin lokaci a haka yayin da shi kuma yake morewa kallonta son ranshi. Hira suka d'an tab'a kad'an, k'ofofin zuciyar Shukhura sun bud'e gaba d'aya suna d'iban sak'onnin da ke samun babban matsuguni a cikinta, da ya tashi tafiya ya dubeta yace. "A taimaka mini a tura mini hotunan da zasu dinga d'ebe mini kewa. “ Ya fad'a ya na me mik'o mata kyakkyawar wayarsa kamar shi, ta fuskanci yadda yake me kyau haka komai nasa yake me kyau. "Aini bana da hoto ko d'aya.“ "Ko a wayar Yayarmu ne a d'an samo mini mana. “ Don a d'an hirar nan da sukai ta ambaci Yayarmu ya kai wajen sau nawa, anan ya gane da wacce take zaune kusa da ita yai tunanin 'yan biyune itace Yayarmun, kuma ya fuskanci akwai soyayya me matuk'ar girma a tsakaninsu. "Yayarmu ba ta da waya ai. “ "Kawai dai rowa za ki mini, tom shi kenan a gaishe mini da su Mamarmu da Yayarmu da kuma k'annenmu. “ "Tom shikenan zasu ji insha Allah, nima a gaisar mini da so Hajiya, da kuma Hajiya Inna.“ Dariya ya yi had'e da fad'in. "Hajiya Inna za ta ji da kyau. “ Tunowa da ya yi darun da ta saka da Hajiya ta sanar mata su Shukhura ba 'yan biyu bane, Hajiya Inna har da kuka don ita har ga Allah ta saka ran samun tattab'a kunnenta 'yan biyu da zasu dinga sanyata farin ciki, sai da Hajiya ta lallab'a ta tace ai ba dole sai 'yan biyu ne ke haifar 'yan biyu ba, sai kiga ma 'yan biyun basu haifa, ita kuwa idan da rabo sai kiga ta haifa mana, Hajiya Inna tace. "To Allah yasa, amma 'yan biyunne suma suna tafiya da gado, shiyasa na fi samun tabbacin da 'yan biyu ce za ta haifa mana 'yan biyu.“ Zaune suke suna fuskantar juna da wani kyakkyawan bafulatani hannuwanta ya rik'o yace. "Yarinyata hak'ik'a ke haske ce a cikin rayuwar TURAKI ke za ki masa Katanga da damuwar da yake ciki a yanzu, za ki zame masa alkhairi, farin ciki, kuma madubin rayuwarsa. Hak'ik'a Turaki ya na cikin matsananciyar damuwa, kuma ina da tabbacin kece kad'ai za ki iya fiddashi daga ciki, kece za ki d'ora murmushin da ya dad'e da barin kan fuskarsa, ina mai kuma tabbatar miki ke haske ce cikin rayuwarsa domin kece kad'ai za ki yaye duhun da ke lullub'e da shi. “ "To ta ya'ya kake ganin zan zame masa haske bayan ban sanshi ba ban san a ina yake ba, ban kuma san a ina zan same sa ba. “ "Nima ban sani ba, amman kuma ina so ki mini alqawari guda d'aya. “ "Wani alqawari ne ka fad'a ina jinka, zan cika maka shi domin ina maka kallo tamkar mahaifina. “ Shafa kanta ya yi had'e da fad'in. "Na yi matuk'ar farin ciki yarinyata, Allah ya yi miki albarka.“ "Aminnn, ina jinka gaya mini alqawarin.“ "Kada ki bud'e k'ofofin zuciyarki ga kowa bare har ki basu muhalli, har sai lokacin da zai bayyana gare ki sai ki bashi gurbi a ciki ki kuma rufeta gaba d'aya, idan kwa ba haka ba akwai wani abu da zai muku Katanga a tsakani. “ "To amma. “ "Ba na so kice komai, tun da kin riga kin amsa mini tun a farko. “ Shiru tayi, ta na son ta sanar da shine ta riga ta yiwa wani wannan alqawarin, gashi kuma ya katseta, yanzu ya za ta yi, meye mafita gareta? "To meye alak'arka da shi, kuma meye sunansa na gaskiya? “ "Kafin na amsa miki tambayar zan sanar da ke ba za ki sake ganina ba daga yau, kuma ansar wannan tambayar da zan baki itace maganarmu ta k'arshe. D'ana ne shi, amman kuma mutuwa tai mana Katanga a tsakani tun shud'ad'd'an zamani, sunansa na gaskiya ALIYU ana kiransa da Aa............ Girgizata Shukhura ta yi had'e da fad'in. "Yayarmu.“ Wanda hakan ya yi sanadiyar farkawarta daga baccin da take wanda tai mafarkin nan a ciki. "Mtsss kin kama kin tashe ni, gashi ban samu ya fad'a mini sunan da ake kiransa da shi ba yadda in ya bayyana gareni zan ganesa, gashi yace daga yau bazan kuma ganinsa ba. “ Ta fad'a ta na me jin haushin yadda Shukhura ta katse mata mafarkinta ba tare da an gaya mata sunan da ake kiransa da shi ba, to kuma da yake ce masa Turaki waye ke kiransa da hakan? Oho ta bawa kanta ansa. "Kiyi hak'uri, Mama ce tace na taso ki ki k'arasa wanke-wanken yankewa na yi a hannuna in omon ya shiga zafi yake mini kuma bakwan ta kusa da kikace a tashe ki, to amman kuma waye kike kiran ba'a gaya miki sunan da ake kiransa da shi ba? “ "Mafarkin da na gaya miki ina yi ne Shukhura, gashi kuma yace daga yau ba zan sake ganinsa ba, bansan ta inda zamu had'u da Turaki ba Shukhura kuma ban san da wata alama zan ganesa ba. “ "Yayarmu na gaya miki fa ki watsi da lamarin mafarkin nan na ki mafarki fa ba gaskiya ba ne. “ "Wani mafarkin gaskiya ne Shukhura, don na ji ance wasu malaman sunce duk mafarkin da za kayi shi da daddare ka sake yinsa bayan sallar asuba gaskiya ne, wannan dalilin ne nake jin nima nawa gaskiya ne, kuma ina jin hakan a jikina.“ "Wai Shukhura Ina Yayar takun take ne.” "Gani nan Mama. “ Nusrat ta fad'a had'e da ficewa daga d'akin Shukhura ta bita da kallo. Washe gari Mustapha ya dawo ya kawowa su Shukhura ita da Nusrar wayoyi sababbi fil a kwalinsu sai walwali suke da shek'i, murna gurin Shukhura da Nusrat ba'a magana yayin da Umma bak'in ciki kamar ya karta, ta sanya Nimha a d'aki tace. "Kin gani ko, sun fara tura ki a gefe tun kan arzik'in ya ratsasu, yanzu in da da kara ai har da ke za'a kawo wayar. “ " Ni ban ji komai ba Umma, nima Saminu yace k'arshen watan nan zai siya mini. “ "Au yanzu yarinyar nan ba ki sallami Saminun nan ba, yanzu ki rasa wanda za ki mak'alewa sai matsiyacin da babu abinda zai iya tsinana mana.“ Turo baki gaba ta yi ta na had'e rai tace. "Wallahi ni Umma shi nake so ba abin hannunsa ba, idan har zai bani soyayya da farin ciki ya gama mini komai, kuma k'arshen satin nan zai turo magabatansa gurin Baba. “ Ta na kawowa nan ta fice daga d'akin don ta san maganar da za ta fito daga bakin Umman ba mai dad'i bace. "Amman ke dai anyi gantalalliyar yarinya, to wallahi tun wuri kije ki sami Babanku ki sanar masa ba kya sonsa don wallahi muddun rai ba za ki auri matsiyacin yaron nan ba, dudu nawa ne albashinsa da zai iya rik'eki, aike wallahi zubin matan manya ne da ke, amman da yake ba ki san ciwon kanki ba kin lik'ewa wanda babu d'igon arzik'i a tattare da shi, banda haka da kin samo mana wanda zamu shiga cikin dukiya mu kwantar da kai a cikinta a kuma daina mana d'agawa da dukiyar da babu tabbas d'in za'a ji dad'inta.“ A haka rayuwa take tafiya har aka shiga watan azumi, soyayyar Shukhura da Mustapha kuwa ta yi k'arfin da ba kwa zato, har an kawo kud'i an saka rana ta na yin candy, Nimha ma Saminu ya kawo kud'inta tare za'a had'asu da Shukhura, babu haukan da Umma ba ta yi ba, Baba kuwa yace ba ta isa ba, ai arzik'i na Allah ne. Nusrat dai har yanzu babu wanda take saurara har ta kaima yanzu in za ta fita nik'af d'inta take mak'alewa a hammata sai taje soro ta d'aura don kar ma a ganta ace ana sonta, sun sha fad'a sosai da Shukhura har tace sai ta gayawa Mama, sai kuma ta kasa fad'a, ita tausayi ma Nusrat d'in take bata gani take kamar da aljani take yin mafarkin nata da take kira gaskiya. Iya da Nimha kuwa sun dinga mata habaici kenan wai Allah ya yi mata nauyin k'afa gashi har za'a aurar da k'annenta biyu ita ko mashin shini ba ta da, ita kuwa ko kad'an hakan ba ya damunta lokacin auran nata ne bai zo ba idan yazo kowa zai sha mamaki. Mama da Baba kuwa Nusrat d'in tausayi take basu, don Baba har rubutu yake yi ya na bata ta sha na taimako ko Allah zai fito mata da nata mijin itama ya had'asu gaba d'aya ya aurar. Yau aka kai azumi na goma, kuma yaune Mustapha ya kawowa Shukhura kayan Shan ruwa, madara ce peak ta ruwa katan uku sai bomvita babban robar uku milo babban gwangwani uku, sai suger k'aramin buhu, k'wai kiret biyar, sai kuma kayan fruit, Iya kuma ya aiko mata da katan d'in maltina da madara, saboda kullum yazo zance har soro take zuwa su gaisa ya d'an bata hasafi, tun Shukhura na jin takaicin hakan da kunya har tazo ta sake gaba d'aya, don lamarin Iya sai du'ai son abun duniyarta har ya fi na daa. sai tsalle take ta na murna, da yazo da daddare tun kafin Shukhura ta fita ta riga ta fita don ta na ankare da hararar da take zabga mata in taje, har k'asa ta tsuguna ta nai masa godiya kamar za ta ari baki. Umma bak'in cikin duniya ya isheta, ta na kallo aka shige da wa'yannan uban kayan d'akin Mama, ita kuwa Saminu kayan fruit kawai ya kawo sai k'wai kiret uku, takaicin duniya duk ya bi ya isheta ta dinga tsine masa albarka, ji take kamar ta rufe Nimha da duka don ta kaici, amman ta ci alwashin daga bikin Nimhan har na Shukhuran babu wanda muddun rai ba za ta zuba ido 'yarta ta fad'a gidan wahala ba 'yar kishiyarta ta tsunduma gidan hutu ai taci baya, za ta yi duk yadda za tai taga wannan auran bai yi ba, ko na Nimha ya yi to tabbas na Shukhura bazai yuyu ba za ta shiga duk inda za ta shiga ba tare da ta nemi taimakon kowa, saboda daga k'arshe wanda ka nemi taimakonsa shine wanda yake k'ok'arin ganin bayanka, tun da ga shinan a fina finan hausa ana yi da kuma littattafan hausa.......... 300 za ku biya domin samunsa cikin sauk'i. NABABA FADILA SHU'AIB GTBANK In kuma katin wayane ku turo ta wannan layin, shaidarki ta biya ma ki turo cikinta. 09037093702 In katin wayane 400 zaku biya. Garab'asa gareku masoyana duk wacce ta sayi wannan littafin za ta sami wanda zan rubuta gaba kyauta, ban yadda ki sayi littafina ki dinga turawa gruop ba, in hakan za kiyi ki sameni a layina muyi magana. Allah ka k'arawa mahaifanmu lafiya da nisan kwana, Amin. #Team KTG #N.W.A [10/8, 3:42 PM] Binta Lawan: *BEBE'ARTH* Wattpad@Rashuna https://my.w.tt/Cjpv9nxoJ9?utm_ *KATANGA* ____________ *SEVINE* San da Baba ya shiga cikin gidan Umma kad'ai ya tadda da Nimha a tsakar gida suna karyawa, tun shigowarsa Umma ke bin akwatin hannunsa da kallo, ganin ya nufi d'akinsa zai ajiye tace. "Babansu wannan akwatin fa? “ Bai magana ba ya shiga ya ajiye kana ya fito ya k'wallawa Mama kira, ta amsa ta fito. "Kin kai mini ruwan wankan?“ "Eh na kai.“ "To bani kwandon da jallabiyata. “ Duk na kai suna can.“ "To sannu Allah ya yi albarka. “ "Amin.“ Tace ta juya ta koma d'aki, har zai shiga band'aki Umma tace. "Babansu magana fa nake kaimin shiru. “ "Ko ma dai ta meye idan kinyi hak'uri za kiji.“ Daga haka yai shigewarsa band'akin. Sai da yai wanka ya shirya, kana ya karya, sannan ya k'wallowa Nusrat kira, da tazo yace. "D'auki wannan akwatin ki kaimin ita gurin Iya. “ Tace."To“ had'e da d'aukar akwatin ta nufi gurin Iya, shi kuma yacewa su Mama da Umma suzo su same shi gurin Iyan ya biyo bayan Nusrat d'in, Iya na tambayarta wannan akwatin fa dai dai lokacin Baba ya shigo yace. "Ni nace ta kawo, ajiye kiyi tafiyarki. “ Ajiyewa ta yi ta juya ta fita, kafin zuwan su Mama Baba har ya farawa Iya bayani da suka zo kuma ya had'u ya d'ora musu bayanin yadda sukai da su Alhj Faruoq, kafin su bud'e akwatin suga meye a cikinta, lesuka ne 'yan ubansu masu matuk'ar kyau da tsada har kala uku, atamfofi ma uku, sai mayafansu da takalma da jaka, Iya murna da farin ciki kamar ta yi me, sai gud'a take. "Kai Amma wannan yarinya akwai goshin arzik'i, duk inda tai arzik'i binta yake da gudu ya na kamota, gashi har yau mune zamu had'a zuri'a da familyn Fanda, ai abin sam barka ne wannan.“ Umma kuwa bak'in ciki kamar ta yi me kawai yak'en dole take don kar ace ta na bak'in ciki, Mama kam shiru tai ba tace komai ba, Babane yacewa Mama. " ga su nan ki ajiyesu kar tai amfani da su, har sai yaron yazo sun fahimci juna, idan ta aminta da shi to, idan ba ta so ba zan mata dole ba, don haka kece mahaifiyarta ke kika san ta yadda za ki biyo mata. “ "Ai ta aminta da shi ma Audu, wace sakaryar ce za ta k'i zuk'ek'en saurayi d'an gidan Fanda, ga kyau ga kud'i ga ilimi ga kuma ladabi da biyayya, ko ni da nake tshohuwa wallahi ya na mugun birge ni, ai ku kwantar da hankalinku aure kamar anyishi an gama. “ Baba baice komai ba ya yi musu sallama ya tafi kasuwa, sai Umma ce tace. "Iya dama kin sanshi ne? “ "Inma ban sanshi ba tun da ya na son jikata aikwa saninsa ya zama dole. “ Shukhura da Nusrat suka d'ago suka kalli mahaifiyarsu bayan sun gama kallon kayan suka had'a baki gurin fad'in. "Mama kayan waye to?“ "Naki ne Shukhura. “ "Nawa kuma Mama?“ Ta fad'a ta na kallon fuskar Nusrat kafin ta mayar dubanta kan Maman, ita kuma tai musu bayani kamar yadda Baba ya yi mata ta d'ora daa. "Ba dole za'a miki ba Shukhura, ba kuma za'a tab'a musu kaya ba har sai kun fahimci juna kin kuma aminta da shi, sunzo sun nemi izini ne sun kuma kawo kayan na gani ina so. Ki tsayar da zuciyarki guri d'aya, kada dukiyarsu ta rud'e ki ko wani abu na k'yale² idan har bai kwanta miki a rai ba, ki same ni ki gaya mini ni kuma zan gayawa Babanku sai a mayar musu da kayansu a basu hak'uri.“ D'aga kai kawai Shukhura ta yi ta na sunkui da kai k'asa, Mama ta mayar da kallonta ga Nusrat tace. "Yayarsu babu wani wanda ya tab'a tunkararki da zancen soyayya ne?“ Kai tsaye tace. "Eh babu Mama. “ Shukhura ce tai saurin d'ago kai ta kalli Nusrat d'in yayin da Nusrat d'in ta galla mata harara, ganin hakan da Mama ta yi ne yasa tace. "Gaya mini Shukhura waye? In ita kunya ta hana ta fad'a. “ "Babu kowa Mamanmu. “ Shukhura ta bata amsa. "To shikenan tun da ba za ku gaya mini ba, idan Babanku ya dawo kwa gaya masa, Allah dai ya had'aku da mazaje na gari.“ Suka amsa da. "Amin." A tare. Da yamma Hajiya Suwaiba tazo gidan su Shukhura, Mama tai mata tarb'a ta mutumci da girmamawa dai² da k'arfinsu, yayin da Hajiya Suwaiba take ta yabawa da karamcinsu, ta kuma samu sirikartata 💯. Kayan kwalliya ta kawo mata tace ita da 'yar uwarta, don Mustafa yace mata ya na jin fa 'yan biyu ne, Inna kuwa daga jin haka har ta fara murnar za'a haifo musu tagwaye. Tun daga kan mayuka na gyaran fata babu abinda babu a ciki, godiya sosai Mama tai mata, ta rakata gurin Iya suka gaisa, Iya yadda kuka san ta gurfana a gabanta tai mata sujjada aikwa da ta tashi tafiya ta ajiye mata then thauthand, murna gurin Iya ba'a magana ta taho filin tsakar gidansu ta na ta rangad'a gud'a ta na shiwa Mama albarka don ta iya haihuwa tunda ta haifo Shukhura jinin arzik'i. Umma na d'aki takaicin duniya ya bi ya isheta, wani malulun bak'in ciki ne ke damunta, yanzu ta na gani su Maimuna zasu fandama cikin daula, don had'a zuri'a da Familyn Fanda kamar ka tako arzik'i ne, haka za'a mashaheta bora a cikin gidan nan da ita da 'yarta, don Shukhura ba kunya ce da ita, idan ta auri jinin Fanda kanta zai k'ara girma ta kuma taka wanda taga dama, tazo ta na d'agawa k'arshe ma komai na gidan ya dawo hannunta, da ace Nusrat ce ta san ba ta da matsala za ta dubeta tamkar mahaifiyarta, Shukhura kuwa babu abinda take hanga cikin idanuwanta banda tsantsar taya mahaifiyarta kishi, idan kwa ta samu wannan power ta riga ta zama sorry a cikin gidan nan daga ita har 'yarta, don haka dole ne ta nemi mafita tun lokaci bai nemi k'ure mata ba. "Wai meyasa kika cewa Mama ba ki da saurayi? Bayan ga Malam Tajo nan kamar zaiyi hauka a kanki kin kuma k'i ki bashi damar da zaizo ya fallasa asirin zuciyarsa. “ "Bazan tab'a bashi damar hakan ba Shukhura. “ "Saboda me? “ "Saboda girman alk'awari. “ "Hmmm Yayarmu kenan, na tambayeki.“ "Tom Allah yasa na sani.“ "Wai Yaya Rj yace yana sonki ne? “ "A'a baice ba, amman na san ya na dawowa zai gaya mini.“ "Baice ya na sonki ba, amman kike wahalar da kanki gurin zaman jiranshi, baki da tabbas d'in soyayyarki a zuciyarsa, bacin haka Aunty Maryam ba za ta tab'a bari ki auresa ba, domin Hidaya take da burin ya aura. Dan Allah Yayarmu kiyi watsi da lamarin Yaa RJ, ki tsayar da zuciyarki guri guda, kina da samarin nan ki basu dama har ki samu gwani a cikinsu, don ni a ganina Yaa RJ b'ata miki lokaci kawai yake yana kuma wasa da hankalinki, tun da shekara uku yace miki zaiyi ya dawo, yanzu a k'aida saura shekara d'aya kenan amman me Hidaya tace, cewa tai saura shekaru biyu ya dawo, ke a tunaninki Baba zai barki har nan da shekaru biyu a cikin gidan nan, ko kuma za ki cigaba da nuna babu wanda ke zuwa yace ya na sonki? Ta yaya kike tunanin zan karb'i lamarin aurena da muhimmanci bayan ke ba kiyi aure ba, har ga Allah ba na son na yi aure na tafi na barki.“ Hannuwan Shukhura Nusrat ta kama ta rik'e da hannu biyu kana tace. "Ni yanzu ba lamarin Yaa RJ ne ke damuna ba, akwai abinda ke damuna, kuma shi yake hanani karb'ar soyayyar kowa. Kada ki damu da lamarin aurena Shukhura, shi aure lokaci ne, kowa da akwai lokacin da Allah ya rubuta mata, babu ruwansa da wannan yaa ce ko k'anwa duk wacce lokacinta ya yi shikenan, haihuwa, aure da mutuwa duk tafiyarsu d'aya ne suna zuwar maka ne a sanda ba kai zato ba ba kai tsammani ba, don haka kada ma ki sake ki saka a ranki don banyi aure ba kema ba za ki ba, kin san Baba ba zai d'auki hakan ba, kar kuma ki amfani da hakan kice Mustapha bai miki ba, za ki cuci kanki ne don ni ba na hango aurena a nan kusa, ina ji a jikina akwai wasu abubuwa da zasu faru, amman bansan meye su ba.“ "Wani lamari ne ya hana ki karb'ar soyayyar kowa a zuciyarki. “ Wayar Mama ce tai k'ara alamun an kira Nusrat tace. "Kinga har ya k'araso ba ki gama shiryawa ba, maza kiyi² ki k'arasa shirin in kin dawo ma k'arasa maganar, kuma ina fatan k'anin nan nawa ya dagargazo miki zuciyarki kafin ki dawo, kizo kiy tai mini hirarsa ina saurare don naga alamun hakan ma tun a waya. “ Murmushi kawai Shukhura ta yi, don har ga Allah muryar Mustapha ta tafi da ita, sakamakon wayar da suka dunga yi, Maryam k'anwarsa ya turo ta anshi number Mama shine yake kiranta suna gaisawa, burinta kawai ta ganshi a fili don ta na fatan ganinsa ya fi jinsa shikwa ya dinga ja mata aji har sai yau da aka kusa cin sati suna wayar sannan yace mata zai zo. Shi d'inne kuwa yazo, don haka a gaggauce ta k'arasa shiryawa ta fita, Nusrat na ta zolayarta, don sun zamo tamkar wasu k'awaye aminai, don dukansu babu wacce za ta daki k'irji tace ta na da k'awa aminiya sai dai k'awar da za'a gaisa a wuce, sune k'awayen kansu, kuma hakan baisa Shukhura ta raina Nusrat d'in ba........ 300 za ku biya domin samunsa cikin sauk'i. NABABA FADILA SHU'AIB GTBANK In kuma katin wayane ku turo ta wannan layin, shaidarki ta biya ma ki turo cikinta. 09037093702 In katin wayane 400 zaku biya. Garab'asa gareku masoyana duk wacce ta sayi wannan littafin za ta sami wanda zan rubuta gaba kyauta, ban yadda ki sayi littafina ki dinga turawa gruop ba, in hakan za kiyi ki sameni a layina muyi magana. Allah ka k'arawa mahaifanmu lafiya da nisan kwana, Amin. #Team KTG #N.W.A [10/8, 3:42 PM] Binta Lawan: *BEBE'ARTH* Wattpad@Rashuna https://my.w.tt/Cjpv9nxoJ9?utm_ *KATANGA* ____________ *NINE* Shukhura ta rasa yadda za ta yi da Iya, don abin nata kullum k'ara gaba yake, don idan taje su gaisa bai bata ko ficika ba samun guri take ta zauna, ranar da tai mata haka kuwa mantawa ya yi ya fito babu kud'i a jikinsa, ba ta tashi ba har sai da yace. "Iya a mini afuwa ban fito da kud'i ba yau, amma gobe insha Allah za kiga sak'o. “ Takaicin duniya ya ishi Shukhura ji tayi kamar ta nitse a gurin da take a zaune don tsabar kunya yayin da Iya kuwa ta wangale baki tace. "Tom shi kenan jikana babu komi, da yau da gobe duk d'ayane.“ Kunji sai kace ajiya ta bashi, wani d'an iskan kallo Shukhura ta bita da shi a ranta kuwa tace. 'Zanyi maganinki wallahi, yadda ko shi kansa Fandan aka ce gashi a soro ba za ki fito ba, ke ko govnor garinnan El Rufa'i akace gashi yazo zance gurina ba za kiyi gigin fitowa ba.' Fuska taje ta siyo me mugun abun tsoro, sai dagurintaa ruwa bayan an idar da sallar asham, dama lokacin ne dai² zuwansa, tun yamma da tai wanka ta saka riga da wando dama, don haka sai ta d'auko hijabinta har k'asa ta sanya, Mama dama ta na d'akin Baba don haka sai ta cewa Nusrat. "Yayarmu bari na fita soro.“ Tace mata. "Tom. “ Iya na ganin giftawar Shukhura ta fasa tayar da sallar da za tai, don yau ta makara ba ta samu bin jam'in asham ba wani bacci ne ya kwasheta ta na zaune. Murmushi ta yi ta ziro silifas d'inta ta biyo bayan Shukhura ta na k'iyasta yau sallamar da za'ai mata me matuk'ar nauyi ce, don ta na bin bashin wancen zuwan. Shukhura na fita soro ta cire hijabinta ta sak'ala shi jikin k'ofa sannan tai saurin d'aura fuskar ta juya baya. Bakin Iya ya k'asa rufuwa har ta doso soron, dama soron gidan gashi da mugun duhun tsiya, ko hucewa za kai sai ka haska saboda gudun masu lab'ewa, zance ma in zasui sai sun kunna fitila. "A'a yau kuma ba ku kunna fitilar ba ne? “ Cewar Iya ta na tsayawa a dai-dai tsakiyar soron gidan don ba ta hangar komai kar taje ta taka wani daga cikinsu shiyasa tai maganar don su kunna fitila, wani irin dank'a Shukhura taiwa kanta ta had'a fuskokinsu guri d'aya ta sauya magana zuwa me abun tsoro. "Ke wata iriyar nanatacciyar tshowa ce, mu ba ma son mutum me son abun Duniya, daga yau idan Mustapha ya k'ara zuwa kika fito sai mun karya tsila tsilan k'afafuwan nan naki masu kama da Babyn roba, kuma mu shanyar miki da b'arin jikinki gaba d'aya. “ Kar kar kar kawai jikin Iya ke yi uwa mazari ihun da taso ta yi ma ta k'asa wani mugun tsoro ne ya shigeta wanda ba ta tab'a jin irinsa ba. Allahumma inni auzu bika minal kubsi wal kaba isi, kawai take karantawa a ranta kafin Shukhura ta buga mata razananniyar tsawa had'e da fad'in. "B'ace mana da gani tun kafin mu mayar miki da k'afafuwanki a sama kanki a k'asa.“ Fitsari ne zirrrr ya fara bin k'afafuwan Iya kafin ta juya a guje sai ji kake k'um ta bugu da bango ta dawo baya, wata wahalalliyar k'ara ta saki, ta na so ta rarrafa ta bar soron ma ta k'asa anan ta zube a sume tsabar tsoro da rikirkicewa. Umma ce ta jiyo k'arar, don haka ta nufo soro da 'yar fitilarta, ta na haskawa taga Iya a sheme cikin fitsari. "Subhanallahi.“ Shine abinda tace kafin ta juya taje ta kirawo su Baba, ruwa aka watsa mata ta farka a mugun tsorace ganin su Baba kawai ta fashe da mugun kuka, Baba na tambayarta abinda ya faru, kawai cewa take su kamata su kai ta gurinta. Babu yadda Baba baiyi da Iya ba akan ta fad'i abinda ya faru da ita tak'i, k'arshe tace ina ruwansa ya rabu da ita don dole ya k'yaleta Mama ta dubi Nusrat tace. "Kika ce Shukhura na soro, ya kuma ban ganta ba?“ "To nidai Mama haka na ji tace mini, to ina kyauta zaton ban jita dai² ba tun da banga ta d'auki tabarma ba ma.“ Ta na rufe bakinta Shukhura na sallama Nusrat tace. "Yauwa ga ma ta nan.“ Kafin su amsa mata sallamar. "Ina kika je? “ Shine tambayar da Mama ta jefeta da ita, sosa kai tai kafin tace. "Mustapha ne ya kirani gashi a k'ofar gidanmu na fito na anshi sak'o, kuma da na fito ban ganshi ba ina jin zolayata yake, shine muka had'u da 'yar ajinmu muka tsaya muna d'an tattaunawa. “ "Ya yi miki kyau." Mama tace mata, Nusrat kuwa ta kafe ta da idanuwa, ita ta san dalilin kallon da take mata akan abinda ya samu Iya ne ta na zargin Shukhuran ce tai mata wani abu, murmushi kawai Shukhura ta yi, don ta san in ta ritsa ta dole ta gaya mata gaskiya. Tun daga wannan ranar Iya ba ta k'ara gigin fita in Mustapha yazo ba, saboda ita kad'ai ta san azabar da ta sha na jinyar goshinta, shi kuwa da yaga kwana biyu ba ta fitowa shine ya cewa Shukhura zai shiga su gaisa da Iya taje ta gayo mata, ko da Shukhura taje kuwa, iya tace ba ta san zance ba, ta yiwa Allah ta yiwa Annabinsa tace masa yasha zamansa ta yafe duniya da lahira, Shukhura kuwa tace ai kuwa sai ya zo ta fita ta na dariya Iya ta banko k'ofarta ta saka sakata tace sai dai yazo ya gaisar da k'ofa alk'ur'an. Kayan toshi ma da aka kawowa Shukhura k'arara Umma ta nuna bak'in cikinta a gurin, duk da Saminu ma ya yi dai² k'ok'arinsa amman ta raina ta na ta tsine masa albarka, ta na kiransa me kantar talauci, azumi kawai take jira ya k'are ayi sallah ta dugunzuma neman mafita, cikin k'udurar Ubangiji akai sallah lafiya aka gama lafiya, aikuwa ta shiga can cikin k'auyen zariya acan ta samo wani malami, ya shaida mata kud'in aikinta dubu ashirin idan har ta kawo dubu ashirin d'innan to tabbas wannan aure bazai tabbata ba, jiki na rawa ta dawo gida ta sayar da kayan gadonta gaba d'aya ta koma ta kai masa yace to yanzu ta koma taje ta kawo masa k'asar da Mustapha ya taka, idan ta kawota to tabbas da kansa zai zo yace ya fasa wannan aure, shi kuma Saminu za mu juyar masa da ra'ayi da kansa zaice ya fasa auran Nimha, kinga daga nan sai mu juyo da hankalin Mustapha kan Nimha. Farin ciki sosai Umma tai da jin jawabin Malamin, aikuwa ranar da Mustapha yazo ta k'asa ta tsare ta na jiran shigowar Shukhura ta yi sauri ta fice ta d'ebo k'asar da Mustapha zai taka, aikuwa ta na ganin shigowar Shukhuran ta yi saurin ficewa ta 'yebo washe gari taje ta kaiwa malamin aikuwa yace ta na kwance za ta ji kyakkyawan labari... 300 za ku biya domin samunsa cikin sauk'i. NABABA FADILA SHU'AIB GTBANK In kuma katin wayane ku turo ta wannan layin, shaidarki ta biya ma ki turo cikinta. 09037093702 In katin wayane 400 zaku biya. Garab'asa gareku masoyana duk wacce ta sayi wannan littafin za ta sami wanda zan rubuta gaba kyauta, ban yadda ki sayi littafina ki dinga turawa gruop ba, in hakan za kiyi ki sameni a layina muyi magana. Allah ka k'arawa mahaifanmu lafiya da nisan kwana, Amin. #Team KTG #N.W.A [10/8, 3:42 PM] Binta Lawan: *KTG* Wattpad@Rashuna https://my.w.tt/Cjpv9nxoJ9?utm_ ____________ *TEN* KWANCI TASHI Gurin Ubangiji ba wuya, su Shukhura har sun yi candy, sati d'aya da yin candynsu aka kawo lefen su. Akwatina 6 haka Saminu yaiwa Nimha, kuma ya yi iya k'arfinsa kayanta babu kushe ko d'aya, Shukhura kuwa akwatina goma sha biyu dank'are da kaya na alfarma, sark'ok'in daham kuwa zasu kai 6 a ciki, nan da nan hankalin Umma ya k'ara tashi, ta fuskanci wannan malamin kawai kud'inta yake ci dole ta canja shik'a. Wani k'ungurmun boka ta kuma samowa shi ya sanar mata. "Duk wanda yace miki wannan aure bazai tabbata ba to tabbas yai miki k'arya, kud'inki kawai yake ci, wannan aure muk'addari ne daga Ubangiji kuma babu makawa sai ya faru, don haka kije ki rungumi k'addarar da tazo miki da hannu bibbiyu.“ "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, yanzu babu wata mafita? “ " Babu wata mafita indai akan hana auran nan ne, sai dai wani da ban kuma, don wannan ba makawa sai ya tabbata. “ Shiru Umma tai hankalinta in yai dubu ya tashi, yanzu dole ta koma ta d'ebi cin kashi gurin kishiyarta, haka za ta zauna ta na kallon Shukhura na d'agawa da fariya ta na auren me kud'i, komai ta yayibo ta kaiwa uwarta ta na zaune kamar jaka, 'yarta kuwa sai dai ta yayibo kantar talaucinsu ta juye mata, ina bazai yuyu ba da sake, to kuma ta ya ya? Koma ta yaya ne ta bawa zuciyarta amsa daga bisani ta kalli bokon za tai magana ya dakatar da ita da hannu d'aya. "Kud'in aikinki dubu d'ari biyu, za ki kawo mini dubu hamsin da bak'ak'en kaji guda shida, idan aiki ya tabbata sai ki ciko dubu d'ari da hamsin, amman idan har kina so aikin ya kama jikinta sosai sai idan babu ran mahaifiyarta. “ 'Ta yadda da ingancin aikin bokan nan, tun da har ya san abinda ke zuciyarta, to amman kuma ta ya ya mahaifiyarta za ta rasu bayan ranta ba a hannunsu yake ba?.' Maganarsa ce ta dawo da ita daga tunanin da ta tafi. "Zan tura mata ciwon da zaiyi sanadiyar mutuwarta, daga nan ba ki da sauran Katanga tsakaninki da Shukhura, ke za ta dingaiwa kallon mahaifiyarta, amman kafin nan sai an fara raba tsakaninsu da me gidanku, a kuma rufe bakinsa, babu case ga wannan tsohuwar matar idan har kina sakar mata abin Duniya. Su kuma 'yan uwanta za'a raba soyayyar da ke tsakaninsu, saboda ta na matuk'ar son su fiye da son da takewa kanta.“ Farin ciki ne ya dabaibaye zuciyar Umma, ta dinga sharara masa godiya, suka rabu akan za ta dawo ta kawo masa abinda ya Buk'ata.“ Akwatinan Nimha ta kwashe da wasu kaya daga ciki taje ta sayar ta kai masa kud'in da kajin da ya buk'ata, ya bata wani ku'ullikan magani, d'aya ta zuba a cikin abincin da Mama za ta ci, d'aya ta zuba cikin ruwan turaren da za'aiwa Shukhura kamu da shi, d'aya cikin abincin da Baba zai ci, sai laya da za ta saka a bayan gadon Shukhuran, babu wanda zai lura da layar sai ita da ta saka da kanta, sauran abubuwan kuma shi zai ji da komai. Shirye²n biki su Mama suke hankali kwance, don yanzu saura sati guda a fara shagul gulan biki, duk da Mama ta fara fuskantar wasu sauye² daga Baba hakan baisa ta tayar da hankalinta ba, da Allah ta dogara shi kuma taci gaba da mik'awa buk'atunta, don a 'yan kwanakin nan wasu mugayen mafarkai take mara dad'in ji ko kad'an, kawai ta na danne damuwarta ne saboda yaranta, don wani abu da Shukhura kuma ta tsira shine, duk dare sai ta sanyata a gaba ta na kuka ta na rok'onta akan a fasa wannan bikin, ta na jin kamar wani babban al'amari zai tunkaro su idan har akayi wannan auran, sai dai ta lallasheta da nasihohi masu ratsa jiki, don babu damar tunkarar Baba da wannan maganar, bare ya dube su, don ita kanta Mama yanzu ba ta buk'atar auran, to Baban gaba d'aya yanzu ya sauya musu da Nusrat kad'ai yake zama ya yi hira, hakan ya kuma tayar da hankalinsu gaba d'aya amman a haka suka daure suka cigaba da shirye shiryen da ba'a rasa ba. Ranar juma'a akai kamu anan cikin gidan, Iya ce ta kama duka amaren guda biyu, yayin da taiwa Shukhura amfani da turaren Nimha, taiwa Nimha da na Shukhura wannan kuma duk tsarin Umma ne. Ranar juma'ar da daddare akai Dinner d'in gidan su Mustapha, da Baba yace Shukhura ba za ta ba, da k'yar Nusrat ta lallab'a shi ya barsu suka je, kuma diner d'in ta k'ayatar da dukkan wanda ya halarci gurin. Washe gari asabar sukayi walima anan cikin gidan don Baba ya hana DJ kuma walimar ta yi gwanin ban sha'awa. Washe gari lahadi kuma aka d'aura auran. Safiya Abdullahi Ahmad da angonta Mustapha Faruoq Fanda Zainab Abdullahi Ahmad da angon ta. Saminu Yusha'u Hamza. Tun da aka d'aura auran Shukhura da Nusrat ke kuka, gaba d'ayansu suna jin wani miki a zuciyarsu ya na musu ciwo amma ba su san dalili ba, Mama ce tai k'ok'arin rarrashinsu duk da itama ba ta jin dad'in jikinta, amman saboda mutanen da ke shigowa ana kallonsu shiyasa ta rarrashesu, su d'aki falle d'aya bare tace su shiga ciki suyi kukan nasu babu wanda ya gansu, ta san dai kukan rabuwa suke, wannan kuka kuwa dole su yishi, sun taso tamkar 'yan biyun da suka zauna a mahaifa d'aya, suna matuk'ar son junansu ko kyauta za'a yi musu sun fi son ayi musu a tare, idan kwa aka bawa d'aya to tare zasui amfani da shi, musamman Shukhura da ki mata kyauta gara kiyiwa Nusrat za ta fi matuk'ar farin ciki, hakan da Mustapha ya gani ne yasa komai zai yiwa Shukhura sai ya yi musu tare da Nusrat , wataran ma Nusrat d'in kad'ai yakewa kyauta don kawai yaga farin cikin sahibarsa. K'arfe biyar dai² aka kawo motocin d'aukar amarya Shukhura, ita Nimha sai bayan sallar Isha saboda babu nisa, a lokacin kukan Nusrat da Shukhura ya k'ara k'arfi suka rungume juna suna kuka kamar ba sa rabu ba, Iya ce tazo ta janye Shukhura ta na sababi. "Meye kuma na kuka bayan Allah ya 'yanta ki ya kaiki gidan daula, ki daina biyewa Nusrat bak'in ciki take miki don ita Allah ya yota me nauyin k'afar tsiya har yau ko mashin shini babu. “ Shukhura kukanta kawai take, Iya ta dank'ata hannun Aunty Maryam suka shiga da ita d'akin Baba, yayin da Mama ta rungume Nusrat ta na jin itama kamar ta fashe da kukan, takai dubanta ga Yusra da take ta aikin matse k'walla, da hannu ta yafito ta itama tazo gareta ta rungumesu ta na jin wani iri a zuciyarta. Nasihu masu ratsa jiki Baba ya yi mata, ban da kuka babu abinda take ta cikin mayafinta daga k'arshe Baba ya sanya mata albarka aka fito da ita, ganin ana k'ok'arin fita da ita yasa ta fisge hannunta ta ruga d'akinsu da gudu, jikin Mama ta fad'a ta ruk'unk'umeta ta na kuka me ban tausayi, ta na jin kamar shi kenan daga yanzu sun rabu rabuwa ta har abada, shafa kanta Mama ta yi, don ta kusa sanyata zub da k'walla kawai ta na jajircewa ne. "Allah ya yi miki albarka Shukhura, kije kiyi hak'uri ki kuma rik'e gaskiya a duk in da kike. “ "Mama ki yafe mini.“ "Babu abinda kika tab'a yi mini Mamana, ko da kinyi mini nan gaba na yafe miki Shukhura Duniya da lahira, fatana ki rik'e 'yan uwanki da daraja, kada ki bada damar da za'a rusa ginanniyar katangar k'aunar da na gino a tsakaninku tun kuna yara, idan kikai mini haka kin biyani Duniya da lahira, Allah ya yi muku albarka baki d'ayanku, Amin, muje maza ana jiranki. ” Ta rik'o hannunta had'e da na Nusrat, don Yusra tun d'azu ta fice k'ilama har ta samu mota, a hannun Aunty Maryam Mama ta kuma dank'a ta had'e da fad'in. "Allah yasa ki shiga a sa'a, insha Allah mutuwa ce za ta fito dake daga wannan gida cikin salama da aminci, Allah kuma ya baku zaman lafiya na har abada amin, Yayarsu kije ki raka 'yar uwarki d'akinta. “ Daga haka ta saki hannun Nusrat d'in ta shige d'aki, daga jin k'arshen maganarta ka san kuka take. Sai da aka kai Shukhura gurin Hajiya Suwaiba da gurin Inna kana aka huce da ita sashenta dake gefen gidan. Sashen Shukhura gaskiya ya had'u iya had'uwa, komai walwali yake da k'yalli, bed room d'inta ma ciki da falo ne, anan aka yi amfani da kayan da Baba ya siya mata, don cewa sukai ba sai an mata komai ba, Baba yace a barshi dai ya siyawa 'yarsa mutumci, ko ba komai itama za tayi alfahari da haka, kamar yadda ko wace amarya ke yi. Kayan da Baba ya yi musu suma ba laifi sun yi kyau iya kyau. Kowa ya watse daga Shukhura sai Hidaya da suke jiran angwaye su zo suma su kama gabansu, tara dai² Mustapha ya kira Shukhura yace gasu a k'ofar gida zasu shigo don haka sai suka k'ara d'an kimkimtsawa suka fito da ita babban falo suka zauna, abokan nasa biyune sai shi cikon na uku, addu'oi aka yi akan Allah ya basu zaman lafiya kana abokan sukai musu sallama suka fita yabi bayansu don ya yi musu rakiya, su Nusrat ma suka tashi zasu tafi, rik'o hannunta Shukhura ta yi gam tace. "Dan Allah Yayarmu kar ki tafi ki barni.“ Ta fad'a jikinta na rawa, hawaye ne ya zirarowa Shukhura haka zalika Nusrat d'inma suka rungume juna suna kuka, karo na farko kenan da zasu nesanta da juna tun tasowarsu, gurin kwanciyarsu d'aya, filon da suke d'ora kai guda d'aya a haka zasui bacci Shukhura ta rungumo Nusrat ta baya, ta gaba kuma Yusra ta rungumeta, gashi yau zasu kwana ba tare da Shukhuran ba, aure kenan me kawoka wata sabuwar bigiren rayuwa. "Kar ki tafi ki barni, ba na son ki barni, ki zauna tare da ni kinji Yayarmu don Allah.“ "Ai muna tare Shukhura, ba wai mun rabu kenan ba, gobe ma insha Allahu zamu zo, ke dai ki rik'e nasihohin da akai miki, azkhar d'in nan na safe da yamma kada ki sake ki wasa haka zalika nafil fili ma. “ Daga haka ta zare jikinta daga nata ta bi bayan Hidaya saboda tun d'azu Mustapha yace su fito abokansa su sauke su a gida, ledar kaza da youghort Mustapha ya bawa Nusrat ta yi godiya ta shiga motar suka tafi shi kuma ya juya cikin gidan. Ya sha rikici sosai da lallami ya lallamata har sukai sallah suka mika godiyar su ga Ubangiji, daga bisani suka d'an tab'a kazar amarcin don dukkaninsu basu saki jiki sun ci ba, sun d'an jima a zaune, ta na kwance a jikinsa ya kanainayeta kana sukai shirin bacci suka kwanta, Mustapha ya hankad'o ni daga d'akin yace mini. "Asuba ta gari kema kije ki huta. “ Don haka na tafi hutawa sai kuma gobe in kun jini...... 300 za ku biya domin samunsa cikin sauk'i. NABABA FADILA SHU'AIB GTBANK In kuma katin wayane ku turo ta wannan layin, shaidarki ta biya ma ki turo cikinta. 09037093702 In katin wayane 400 zaku biya. Allah ka k'arawa mahaifanmu lafiya da nisan kwana, Amin. #N.W.A #Team KTG #Sonso fisabilillah [10/8, 3:43 PM] Binta Lawan: *KTG* Wattpad@Rashuna https://my.w.tt/Cjpv9nxoJ9?utm_ ____________ *ELEVEN* (ZANEN K'ADDARA) A wannan dare su Nusrat basui bacci ba, zazzab'i ne me zafin gaske ya rufe Mama da kuma matsanancin ciwon kai, wanda bacci ya k'auracewa idanuwanta, haka zalika ma Nusrat ba ta iya rintsawa ba ko kad'an har garin Allah ya waye. Fitowa ta yi ta nufi d'akin Baba don ta sanar da shi sai taji muryar Umma tace. "Nusrat.“ Juyowa ta yi ta na kallonta don ba magana ce ke had'asu ba, face gaisuwa idan Nusrat d'in ta gaisheta. "Cewa na yi Shukhura kuwa ta kiraku? Kinga ni har ta kirawo ta gaisheni." "Ai tun da nai sallar asuba mukai waya da ita. “ Nusrat ta ba ta amsa, don yanzu ba lokacin da za ta tsaya yin tunani akan maganar ba ne, d'akin Baba tai shigewarta, ya na kishin gid'e bacci har zai fara fusgarsa ya ji alamun shigowar mutum, a hankula ya sauke idanuwansa akan fuskar Nusrat yace. " 'Yar baiwa lafiya? “ "Baba, Mama ce ba ta da lafiya tun cikin dare. “ "To sai akai ya ya kuma. “ Tsura masa ido Nusrat tai, kamar ba Baban nan nasu ba, mai k'aunar mahaifiyarsu, ta hango lokacin da tai wata rashin lafiya yadda duk ya firgice ya fita daga hayyacinsa, ya zamo tamkar shine mara lafiyar. Wani yahu me tauri ta had'iye tace. "Dama chamise zamu je. “ "To sai kun dawo don ni ficika ba na magani. “ Ba tace komai ba ta juya ta bar d'akin, dama ba kud'insa suke buk'ata ba, kawai dai ta gaya masa ne a matsayinsa na me jagorantarsu gaba d'ayansu. Umma kuwa bak'in ciki ne yai mugun kama ta da taji wai Shukhura sun yi waya da Nusrat, a yadda bokanta ya sanar mata idan har Shukhura ta kwana a kan gadon nan to sunyi rabuwa ta har abada ita da 'yan uwanta, tsakaninsu kuwa sai dai kallo, ita kuwa Mama na mutuwa, to tabbas ita za ta zamo mahaifiyar Shukhura kuma babu wanda ya isa yai magana akan hakan, dad'inta d'aya ne da ta fuskanci Mama ba ta da lafiya, tsakanin Shukhura da Nusrat kuma za ta zuba ido ta gani. Sun ci sa'a me chamise d'in ya fito, ya yi mata allurar zazzab'i ya bata kuma magun guna, kud'i ya kama 1500 Nusrat ta bashi 2000 ya basu cangin 500 suka kamo hanya suka taho gida. To Alhmdlillh sai jikin nata ya d'anyi sauk'i kad'an, har Nusrat ta had'a mata shayi me kauri ta sha, ganin jikin Maman ya yi sauk'i sai a sannan ta yi tunanin Shukhura har yanzu ba ta kirasu ba, amman gashi ta kira Umma sun gaisa, ta na cikin wannan tunanin sai ga Hidaya ta shigo tace mata tafiya zasuyi, amman zasu fara biyawa gidan Nimha da Shukhura in da sak'on da za'a kaiwa Shukhura a bada, kafin Nusrat ta mik'e ta bawa Hidaya sak'on sai wayar Hidayan ta yi k'ara sai Hidayan cewa ta yi. "Kinga ma Shukhuran na kirana bari muji meye to. “ Ba ta jira me Nusrat d'in za tace ba ta d'aga wayar, ta can b'angaren Shukhura tace. "Hello Hidaya kice a had'o mini duka akwatinana ku taho mini da shi.“ "To, shi kenan za'a taho da su, ga Nusrat za tai miki magana. “ Hidaya ta fad'a don ganin kallon da Nusrat d'in take mata, alamu ne na ta na son magana da 'yar uwar ta ta, k'ittt kike ji Shukhura ta kashe wayarta mamaki gaba d'aya ya kama su, a haka Nusrat ta shiga had'awa Shukhura duka akwatinanta da abubuwan da ba'a rasa ba, suka samo yara duk suka fita da su aka zuba a mota, kana sukai sallama da su Hidayan Nusrat tace. "Ku gaishe mini da Shukhuran ku gaya mata Mama ce ba taji dad'i ba." A tunanin Nusrat idan aka cewa Shukhura Mama ba taji dad'i ba za ta kira waya, in ma fishi take da ita ko tai mata wani laifin da ba ta sani ba ai ta kira layin Maman ta ji, amman har dare Shukhuran ba ta kira ba, ganin yadda duk Nusrat d'in ta bi ta damu yasa Mama tace. "Bani wayata na kirata. “ Saboda tun d'azu Mama tace ta kirata tak'i, saboda ta na ganin kamar ta na da dalilin da yasa tak'i nemansu gara su d'an d'aga mata k'afa su gani. “ Ringin d'aya Shukhuran ta d'aga da murnarta tace. "Hello Ma.......“ Cak taji maganarta ta tsaya ta kasa furta Maman da take buk'atar fad'a, Mama ji tayi gabanta ya yanke ya fad'i a hankula ta furta. "Innalillahi wainna ilaihir raji'un.“ Kafin taji saukar kukan Shukhura a kunnenta. "Shukhura lafiyarki kuwa?“ Cikin kuka tace. "Nima ban san me ke damuna ba, daku na kwanta a raina da ku kuma na tashi, tun da mukai sallar asuba nake son kiran wayarku amman na k'asa, sai na ji ana rad'a mini a kunnena wai ke ba mahaifiyata bace, Umma ce mahaifiyata ko kuma ace su Yayarmu ba 'yan uwana bane Nimha ce kad'ai 'yar uwata, na san Yayarmu ta damu sosai amman wallahi ko muryarta ba na son jin, ina cikin damuwa zuciyata ta na mini zafi, da na san haka auren zai zo mini da babu abinda zai sakani yinshi. “ Ta na kawowa nan ta fashe da wani matsanancin kuka, Mama kuwa Innalillahi kawai take ambata a zuciyarta, yayin da Nusrat duk ta na jin abubuwan da Shukhuran ta fad'a, had'a kanta tai da guiwa ta fashe da kuka me ciwo, 'yar uwarta da take sonta fiye da son da takewa kanta yau itace ta furta ba ta son jin muryarta, me yake shirin tunkaro rayuwarsu ne, waye me buk'atar rusa Katangar farin cikin da suka dad'e da ginata a zuciyoyinsu? Majina Shukhura ta jaa taci gaba da cewa. "Mama kicewa Umma me mukai mata take son rusa rayuwarmu gaba d'aya, in wani abu mukai mata sai mu nemi yafiyarta, na san dai itace ta shiga tsakaninmu saboda da sassafe ita na fara kira na gaisar, bayan ko anan cikin gidan ba kullum nake gaisheta ba. “ Numfasawa Mama tayi tace. "Umma ba ta isa ta miki komai ba Shukhura, ki saka hakan a ranki, babu wani abu wanda yake faruwa a rayuwa face dole sai da wani zare da ya haddasa hakan, kuma bama iya ganin zaren, shi wannan zaren shi ake kira ZANEN K'ADDARA. Dan haka kada ki kuma danganta abinda ya same ki da wani d'an adam, duk abinda ya sameki to ki tabbata yana cikin k'addararki, ki kuma kai kukanki ga Ubangiji domin shi kad'aine zai baki ikon cinye jarabawar da yai miki har ya yaye miki abinda ke damunki, yanzu kije kiyo auwala ki d'auki qur'ani ki karanta za kiji sanyi a ranki, maza jeki, Allah yayi miki albarka, ki kuma daina wannan kukan.“ Muryarta can k'asa tace. "Tom“ Mama ta kashe wayar ta lumshe idonta kana ta bud'esu akan Nusrat da ke gurshek'an kuka...... Jiya ba ku jini ba, chargi ne ban samu ba wutarmu ta lalace, gobe da jibi ba lallai ne ku jini ba saboda muna hidimar biki. 300 za ku biya domin samunsa cikin sauk'i. 0567838462 NABABA FADILA SHU'AIB GTBANK In kuma katin wayane ku turo ta wannan layin, shaidarki ta biya ma ki turo cikinta. 09037093702 In katin wayane 400 zaku biya. Allah ka k'arawa mahaifanmu lafiya da nisan kwana, Amin. #N.W.A #Team KTG #Son so fisabilillah[4/26, 8:42 PM] Rabi: BEBE'ARTH Wattpad@Rashuna KATANGA... ............... 12 Cikin dare sosai jikin Mama ya tsananta kwana sukai basui bacci ba washe gari aka nufi asibiti da ita, suna zuwa ruwa aka fara saka mata don ta jigatu sosai, kafin a fara gwaje gwaje da aune aune wanda kuma basu hango komai dake damun Maman ba don haka suka rubuta musu tasa tasai. Nusrat ce kad'ai ke jigila da Maman dukkan abinda aka buk'ata da kud'in Maman take yi don tun tahowarsu babu wanda ya biyo bayansu. Typod da Maleria ce ke damunta har ta kusan cin k'arfinta don haka aka shiga mata treatment inta zuwa washe gari jikin nata ya d'an samu ba laifi sai bacci take sha abinta ganin hakane yasa Nusrat ta barwa na kusa da su ajiyarta akan zata je gida ta daho, tana fitowa ta samu d'an sahu har k'ofar gida ya ajiyeta ta bashi kud'insa ta shiga ciki, tana jin Iya na k'wallo mata kira don taga giftawarta amman tai biris kamar ba taji ba, tana shiga gurinsu da Umma ta fara cin karo d'an zaburowa tayi tana kallonta kafin tace. ‘’Ta rasu?‘’ Mamaki ne ya kama Nusrat ‘’To me take nufi‘’ Shine abinda zuciyarta ke tambayarta banza tayi mata ta saka kai za ta shiga d'akinsu taji muryar Baba ya k'wallo mata kira. ‘’Ke 'yar baiwa zo nan‘’ Fasa shiga d'akin ta yi ta juya zuwa d'akinsa, so yake ya tambayeta ya jikin Maman amman bakinsa yayi nauyi. ‘’Kiyi hak'uri kinji, Allah yayi miki albarka.’’ ‘’Amin‘’ Tace tana dabarar goge k'wallar dake k'ok'arin zubowa kafin ta kuma cewa. ‘’Jikin nata da sauk'i ma, bacci na barota tana yi.‘’ ‘’To masha Allah, Allah k'ara mata lafiya‘’ ‘’Amin‘’ Tace kafin ta mik'e ta bar d'akin, Yusra ta tarar tana ta malelekuwa a tsakar d'aki, tana ganinta ta taso da gudu ta rungumeta. ‘’Yayarmu ya jikin Maman?‘’ ‘’Da sauk'i,lafiya na ganki haka?‘’ ‘’Yunwa ce Yayarmu rabona da abinci tun d'umaman jiya da safe, akwai garin amman ba kud'in cefane Baba bai samo ba ita kuma tak'i girkawa ni kuma na duba babu ko ficika a d'akin nan‘’ 200 ta cira ta bata kafin tace. ‘’Ki anso taliya gidan tabawa kizo kici, amman ki sauri don tare zamu koma kya dinga ragen da wani abu kafin a sallamomu.‘’ ‘’Tom‘’ Tace tana mik'ewa ta d'au hijabinta ta fice ita kuma ta fara tub'e kayanta da hanzari don duk hankalinta yana kan Mama, bayan fitowarta daga wanka tana ganin Umma da Iya a d'akin Baba tana jin ko tambayarsa jikin Maman suke su dai suka sani ta fad'i hakan a ranta, tana jin Umma na fad'in. ‘’Mutum sai wani fad'in rai yake, sai kace mu muka saka masa nauyin k'afar to sai dai bak'in ciki ya kashe shi aurene dai an riga anyi.‘’ Ko d'aga kai ta kalleta ba tayi ba ta shige d'aki saboda ba maganganunta ne a gabanta ba, a gaggauce ta shirya, ta d'aukarwa Mama kaya da hijabai, sai 'yan abubuwan da ba zaa rasa ba da zasu buk'ata a can, har ta gama had'a komai Yusra ba ta gama cin abinci ba. ‘’Ke matsalata da ke kenan wani yaron ma yafi ki saurin cin abinci .‘’ ‘’Na ma k'oshi Yayarmu bari na wanko hannuna.‘’ Muryar Iya taji tana cewa. ‘’ Mik'o min na cinye Yusra.‘’ D'aukar kwanan tayi ta fita, almajiri taji yana bara ta kwa k'wallo masa kira yana zuwa ta juye masa ta wanke hannunta tana jin Iya na ta sababi tqna tsine mata tai banza da ita ta shige d'aki hijabinta ta d'auka had'e da fad'in. ‘’Muje Yayafmu.‘’ Fitowa,sukayi Nusrat ta kulle d'akin, suka lek'a d'akin Baba ta mishi sallama had'e da ajiye masa 500 tana jinsa yana ta sanya mata albarka..... 200 ne kacal katin waya 300 ga masu buk'ata zasu turo ta wannan accaunt in. 0567838462 FADILA SHU'AIBU NABABA GT BANK In katin wayane ki turo ta wannan number 09037093702, shaidar ki ta biya ma ki turo cikinta #NWA #KTG [4/26, 8:42 PM] Rabi: BEBE'ARTH Wattpad@Rashuna KATANGA... ...............13 Washe gari sai Mama ta tashi jikin nata da d'an dama, har wanka tayi ta sauya kaya suna ta hira da su Nusrat wanda farin ciki duk yabi ya dabaibayesu sunga Maman nasu ta samu sauk'i. ‘’Yayarsu kin gayawa Shukhura kuwa muna asibiti?‘’ Mama ce takewa Nusrat wannan tambayar yayin da Nusrat tace. ‘’Na kirata ba ta d'aga ba ni kuma ban kuma kira ba.‘’ ‘’Kar kice zaki fishi da ita, domin kece zaki zame musu mahaifiya yayin da bana duniyar, nidai ina dad'a baki hak'uri, ki zamo mai hak'uri ga k'annenta, kirawo mini ita a wayata ki bani.‘’ Ji tayi ta kasa yiwa maganar Maman fassara taji kalaman wani iri a k'wanyarta, cikin wannan tunanin ta lalubo number Shukhura ta danna mata kira, tana fara shiga ta bawa Mama wayar sai da ta kusa katsewa sannan aka d'aga, cikin sanyin murya ta furta. ‘’Mamanmu‘’ ‘’Na'am Mamana, nayi kewarki‘’ cewar Mama, yayin da Shukhuran tace.‘’Nima nayi kewarki, kina nan lafiya Mama, wallahi wani mugayen mafarkai nakeyi.‘’ ‘’To dai yanzu Alhmdlillh, amman ina kwance a asibiti, ki rik'e addu'oi insha Allah babu abinda zai faru, so nake na ganki idan zai yuhu ko da daddare ne kisa ya kaho ki.‘’ ‘’Tom shikenan insha Allah zamuzo tare, a turon addres in asibiti.‘’ ‘’Toh Allah ya kawoku ya yiwa rayuwa albarka.‘’ ‘’Amin Mamanmu‘’ta fad'a a sanyaye. Suna gama maganar da Mama ta lalubi number Mustapha ta kirashi, yana ganin kiran nata ya kashe ya biyo‘’Ba dai jikin bane‘’ Ya jefo mata tambayar da yake ya fita ya barta da zazzab'i a jikinta. ‘’Uhhm uhmm ya ma sauka, Mama aka kwantar a asibiti, shine tace tana son ganina‘’ ‘’Toh subhanallah ganinan zuwa‘’ Bai jira cewarta ba ya datse kiran. Sai da ya fara zuwa sashen H Suwaiba da H Inna ya gaya musu, duk suka ce bara su shirya kafin su fito suma suje su dubata. Da tagumi hannu bibbiyu ya tarar da Shukhuran da sassarfa ya k'arasa gareta yana cire hannuwan nata had'e da fad'in. ‘’Kin san fa ba'a son yin tagumi.‘’ ‘’Bani da wani zab'i da ya wuce na tagumin sam wani iri nake jina duniyar ba ta mun dad'i.‘’ ‘’Ki kwantar da hankalinki insha Allah Mama za taji sauki', muje ki sako hijabi mu tafi, Hajiya da Hajiya Inna sunce zasu. Iya, Umma, Mmn Amima (Matar Baffa Shamsu)suka zo duba Mama a motar Baffa Shamsu, shi ya kawo su ma, sam basui tsamnanin zuwansu ba tun da har yau kwanansu biyu da zuwa, su na shirin tafiya sai ga su Shukhura nan suka koma suka zauna ana ta gaishe gaishe, Iya sai shishshigewa H Inna take, Shukhura kuwa gefen Mama taje ta zauna suna dad'a gaisawa, daga d'aya gefen Maman Nusrat ce ta sunkui da kanta k'asa tana wasa da gefen hijabin Yusra da tayi matashi da cinyarta tana bacci cikin sanyin murya ta ambaci sunanta. ‘’Yayarmu‘’ 'Dago kanta tayi wanda suka cika da ruwan hawaye tana kallon Shukhuran, to itama Shukhuran nan da nan nata idon ya kaho ruwa, Baffa Shamsu ne ya lek'o yayiwa su Umma magana akan su yake jira don haka sukayi musu sallama suka fita, Hajiya Suwaiba ma sallamar sukai musu ta ajiyewa Mama dubu ashirin a sayi magani da ita, Mama ta dinga godiya to Mustapha ma dubu hamsin ya bawa Nusrat a hannunta ta rik'e ko wani abu zai taso suka tafi suka bar Shukhuran sai dare zaizo ya d'auketa. Hira sosai aka sha tsakanin Mama da tagwayen yaran nata wanda yawanci kalaman Maman kamar nasiha take musu akan su rik'i junansu suci gaba da gina katangar da ta gino musu tun a yarinta, ta had'e hannuwansu duka su ukun ta kalli Nusrat tace. ‘’ Yayarsu kece babba kimin alk'awarin kula da rayuwar k'annenki baza ki bari sui kuka ba, zaki zame musu katangar da zasu jingina da ita.‘’ ‘’Na miki alkawari Mama, amman me yasa kike irin wa'yannan maganganun?‘’ Me makon ta bata amsa kawai sai tayi murmushi ta kalli su Shukhura. ‘’Ku mini alk'awarin mayar da yayarku tamkar mahaifiyarku, ku gaya mata damuwarku ni na tabbata za ta share muku hawaye don baku da tamkarta.‘’ ‘’Mun miki Mama‘’ Suka had'a baki ita da Yusra gurin fad'a ‘’Masha Allah, ku rik'e zumunci, ku rik'e mahaifinku, da 'yar uwarku Nimha, Yayarsu ki had'a kawunanku kuyi zumunci sosai, kar ku rik'e abinda wani yayi muku kuk'i zumunci da shi, kuyi zumunci da shi domin Allah ba don halinshi ba. ‘’Mama kina tayar mana da hankali, kalamanki kamar wasiyya kike yi mana.‘’ ‘’In wasiyar ce ma na gode Allah Shukhura da ya bani damar yi muku,ita mutuwa rigace a jikin kowa,dama haka yake ko na rigaku tafiya ko ku rigani, fatana idan ta Allah ta kasance gareni ku rik'e junanku ku kuma rik'e zumunci ku d'auki jimirin yi mini addua to zan kwanta a kabarina cikin salama.‘’ Dukkaninsu shiru sukai ko wanne da abinda yake sak'awa a ransa, amman har lokacin hannunsu a dunk'ule yake har na Maman tana binsu d'aya bayan d'aya da kallo. Hankalin Umma in yayi dubu ya tashi, ita da boka yace muddun Shukhura ta kwana a gadon nan ta musu Katanga da 'yan uwanta to ya hakan bai faru ba, dole ta koma gurin bokan nan, kuma tana son ma dangin mijin nata ta mallakesu suma su dingai mata kallon babar Shukhuran, yanzu tana ji tana gani ji kud'in da sirikar Shukhuran ta ajiyewa Mama, shima Mustaphan wa yasan adadin nawa ya bawa Nusrat in,don haka ta yanke gobe da sassafe can gurin bokan nata za tayiwa tsinkayi. ~WASHE GARI~ Ta gurfana gaban boka kamar wacce ke shirin yi masa sujjada, bayan ta gama zayyana masa abinda ke tafe da ita. ‘’ Kin fiya gaggawa in baki wasa ba aljani bela zai fatattaki aikinki gaba d'aya daga nan gurin.‘’ Cikin rawar murya Umma tace. ‘’ Allah ya huci zuciyar aljani bela, na tuba kaina bisa wuya, idan aiki ya kammala na maka alk'awarin dubu d'ari biyar.‘’ ‘’Aljani Bela yaji dad'in kyautar da kikai masa don haka yace ki koma gida ki kwantar da hankalinki, kina zaune zakiga al'amura suna canzuwa hatta sirikan nata sai sun dawo gurfana miki.‘’ ‘’Godiya nake, godiya nake aljani Bela.‘’ Ta fad'i hakan tana barin gurin da baya da baya..... 200 ne kacal katin waya 300 ga masu buk'ata zasu turo ta wannan accaunt in. 0567838462 FADILA SHU'AIBU NABABA GT BANK In katin wayane ki turo ta wannan number 09037093702, shaidar ki ta biya ma ki turo cikinta Duk wacce za ta sayi littafina ta sayeshi da sharad'in in na mutu ban k'arasa ba ta yafe mini da rai da rayuwa duk a hannun Allah suke, bani da tabbacin zan kai lokacin sai dai muna fatan fin hakanma, Allah kasa mu cika da imani amin. #NWA #KTG [4/26, 8:42 PM] Rabi: BEBE'ARTH Wattpad@Rashuna KATANGA... ...............14 Rashin zuwan Baba sosai yake damun Mama amman ba ta fito ta gaya musu ba, amman abin yana mugun bata mamaki ainun,amman duk da hakan ta nayi mishi uzuri may be wani abu ne ya hana shi zuwa, amman yau tabbas za ta saka Nusrat ta kira mata shi, don tana son su gana kafin ta Allah ta kasance a kanta, don wannan ciwon nata ba ta jin na tashi ne, da mugun zazzab'i ta kwana, sai da gari ya d'an sha sannan ya sauka gashi yanzu ma tana jin alamun dawowarsa, kallon Nusrat tayi tace. ‘’ Yayarsu yau in kinje gida kicewa Babanku yazo ina son ganinsa .‘’ ‘’Tom insha Allah zan gaya masa, jikinne naji muryarki wani iri?‘’ ‘'Zazzab'in ne yake son dawo mini kin sanshi da naci'’ '‘Sannu, insha Allah ma bazai dawo ba, ni wallahi har ina saka ran sallama ma da naga jiya jikin naki yayi kyau'’ ‘’Wallahi nima haka Yayarmu, har na fara murna zaman asibitin nan sam ba dad'i‘’Cewar Yusra. ‘’Zaman asibiti ina yaga dad'i ai sai dole sai kuma ta kama ka, bari naje gida yanzu don na dawo da wuri, ki kula da Maman.‘’ ‘’Tom shikenan sai kin dawo, ki tahon da wani kayan na sauya wannan.‘’ ‘’Tom‘’ Kafin ta matsa jikin gadon tace. ‘’Mama na tafi‘’ ‘’Tohm sai kin dawo, kar ki manta ki kirawo mini Baban naku.‘’ ‘’Insha Allah, na san bai fita ba ma tun da yanzu goma tayi.‘’ Tana kawowa nan ta saka kai ta fice. Ta kwa samu Baban a gida, d'akinsa ta fara shiga suka gaisa kana ya tambayeta jikin Maman tace ‘’Da sauk'i, tace ma in ka samu dama kaje tana son magana da kai.‘’ Shiru yayi kamar bazai ce komai ba daga bisani ta numfasa yace. ‘’Na rasa me yake damuna ne wallahi, sam bana jin dad'in jikina in zauna inyi rubutu ma in sha abin ya gagara amman bara ki gani‘’ daga haka ya nufi ma'ajiyarsa ya lalibo wata takadda, ya d'auko alk'alami da tawada da allo ya mik'o mata. ‘’Ungo maza rubuta mini ita yanzun nan na sha. ‘’ Karb'a tayi had'e da amsa mishi da ‘’To‘’Kafin ta gyara ta fara rubutun, to da yake tana da saurin rubutun sai nan da nan ta gama ta wanke masa, ya karb'a yayi bismilllah ya shanye tas yayi hamdala. ‘’Ki tafi da takaddar ki ajiye a gurinki, in kin samu lokaci ki dinga rubutawa insha Allahu ba dai mutum yayi tasiri a kanki ba.‘’ ‘'Tohm na gode '’ Cikin hanzari tayi duk abinda za tayi ta koma asibitin tana zuwa ta tarar da jikin Maman sosai ya rincab'e likitoci ne ma a kanta, Yusra na gefe tana kuka. Likitan ne ya juyo ya kalli Yusra yace. ‘'Ina me jinyar nata?‘’ Kafin Yusran tace wani abu Nusrat tayi saurin cewa. ‘’Gani nan‘’ had’e da shigowa ciki. ‘’Ana buk'atar jini da hanzari, don zazzab'in ya k'one mata jini.‘’ Cikin tashin hankali Nusrat tace da shi. ‘’To a ina zan samo jinin?‘’ ‘’Baza kije ki tambaya ba ko ni kike so na rakaki?‘’ Yace mata a kausashe, girgiza masa kai tayi had'e da ficewa da hanzari k'walla na taruwa a idanuntaa, da tambaya ta samu ta isa d'akin da ake sayar da jinin, tana zuwa suka tambayeta wani gruop za'a bata, sai a sannan ta tuna shaf ta manta jininma kala kala ne baki na rawa tace musu bara ta koma ta tambayo, har da gudu gudu ta had'a tana haki tana tambayar likitan kafin ya gaya mata sai da ya balbaleta da masifa. ‘’Ke wata irin dak'ik'iya ce tun kan ki tafi ya kamata ki tambaya, idan kika jaho ta rasu ai bani nayi asara ba , kice 'O' zasu baki.‘’ ‘Ai ba ta bari ya rufe bakinsa ba ta kwasa da gudu ta na ayyanawa a ranta da Shukhura ce sai dai su d'ebi 'yan kallo da likitan nan, don taga alamun tijararre ne tun zuwansu ake fad'arsa har ba'a so dutynsa ya kama itama taso kafin zuwansa an sallamesu don ba ta son hayaniya. Sai da ta koma ta kuma tuna ba ta tambayeshi guda nawa ba, kawai ta amso leda biyu ta juyo, tana zuwa ya ansa yana b'alla mata harara yaje ya sakawa Maman inda Allah ya taimaketa dama biyun ake buk'ata, guri ta samu tana mayar da numfashi 'yan gefen gurinsu sai sannu suke mata Yusra kuma ta d'auko ruwa ta bata. ‘’Na gode.‘’ Tace da ita tana cisge bakin ledar ta hau sha. Ana fara sakawa Mama jinin ta samu bacci, sai kuma ga Baba yazo, baiji dad'i ba da ya tarar tana bacci amman sai ya kasa tafiya yaja kujera ya zauna daga gefenta yana jiran ko za ta farka, ganin Baban ya zauna yasa Nusrat da Yusra suka fita harabar asibitin sai gashi sun ci karo da Nimha da mijinta suna ta zagayen neman inda suke, gaisawa sukayi suna tambayarsu me jiki su kuma suna basu amsa kafin suce suzo su shiga ciki su ganta duk da bacci take, suna shiga kuma sai suka tarar ta farka suna magana da Baba, wanda yafiyarsa take nema, tana bashi amanar yaranta, shi kuma sai kwantar mata da hankali yake yana alak'antamagan ganun nata da zafin ciwo ne. Cike da tausayawa Nimha ta k'arasa gaban gadon tanaiwa Mama sannu, Saminu kuma ya durk'usa gaban Baba suna gaisawa kafin itama ta tsuguna ta gaisheshi, basu wani jima ba sukai musu sallama suka tafi, bayan sun ajiye lemon zak'in da suka kawo ana ta musu godiya, Baba kuwa ranar har dare yakai a asibitin da ya motsa za ta rik'e shi, sai da dabara yake zuwa yayi sallah ya dawo. Tun daga wannan rana ya zamto kullum sai an k'arawa Mama jini leda uku, saboda zazzafan zazzab'in da take fama da shi, shi yake k'one mata jinin. Duk kud'in hannun Nusrat sun k'are, duk wani abu da za'a amfana da shi a d'akinsu ta siyar saboda siyan jini, hatta wayarta ma ta siyar ta Mama ce kad'ai a hannunta, gashi har ta kai yau babu kud'in da za'a siyi wani jinin, ga Shukhura tun zuwan da sukayi d'in nan ba ta dawo ba, ta kirata yafi sau a k'irga ita da Mustaphan babu wanda ya d'aga bare ya biyo. ‘’ Yusra ungu d'ari biyun nan, ki hau mota maza kije gidan Shukhura ki gaya mata halin da muke ciki tun kafin azo buk'atar jinin nan.‘’ ‘’Tohm‘’ tace tana karb'an kud'in ta tashi ta fita. ‘’Yayarsu.‘’ Taji Mama na kiranta da muryarta da ba ta fita sosai yanzu, matsawa tayi sosai kusa da ita, ta kamo hannunta had'e da fad'in.‘'Sannu Mama’' ‘’Kiyi hak'uri Yayarsu, ki kula da rayuwar Yusra, Allah ya azurtaku da miji na gari yayi muku albarka baki d'ayanku.‘’ ‘’Amin, ki daina irin magan ganun nan, insha Allah zaki ji sauk'i mu koma gida ‘’ Murmushi kawai tayi mata, murmushin da ita kad'ai tasan ma'anarsa. Allah Allah take Yusra ta dawo tun kafin a buk'aci jinin nan, tun da ta riga tayi amannar ko Shukhuran ba ta biyota ba za ta bayar da wani abu a kawo musu, amman ga mamakinta sai taga Yusran zik'au sai magana mara dad'i da tazo mata da ita, cewar Shukhuran tana bud'e k'ofarta taga Yusran ta mayar ta rufe, babu bugun da ba tayi ba tana kuka tana magiyar ta bud'e had'e da gaya mata halin da suke ciki amman tak'i ta bud'e, Innalillahi take ambata a zuciyarta tana jin wani mugun rad'ad'i tun daga can k'asan ruhinta, tashi tayi ta fita daga asibiti ba tare da ta san ina ta nufa ba, kawai dai taga ta tari me napep tayi mishi kwatancen gidan Shukhuran, tana zuwa me gadi yake sanar mata yanzu aka fita da Shukhuran asibiti, sakamakon farfasa kayan gidan da tayi. Jiri taji yana neman kayar da ita, da sauri ta jingini da bango tana dad'a ambaton innalillahi. Me yake shirin faruwa da su ne, wata k'addara ce ta kutso cikinsu ba tare da sun shirya mata ba ?Babu babu babu me bata wayannan amsoshin. Ko ina ta samu jefe k'afafuwanta take ba ta da ko biyar da ta rage mata wacce za ta hau mota ta mayar da ita asibitin, ga wani bak'k'k'irin d'in hadari da ya,had'o ta gabas ana ta iska da walk'iya, iskar sai kokarin cire mata hijabi take, ba ta damu da hakan ba ita dai duk inda ta samu jefa k'afafuwanta take, har ruwa ya saukko taci gaba da tafiyarta cikin ruwan wani me adai daita ne ta bashi tausayi ya tsaya a gabanta yace ta hau, godiya tayi masa ta shiga har lokacin k'irjinta wani irin zafi yake mata da tiriri ga gabanta da,yake ta mugun fad'uwa ko kad'an innalillahi ba ta bar lab'b'anta ba, tana shiga d'akin da suke Yusra ta taho da gudu ta rungumeta tana kuka. ‘’Yayarmu, Mama mama mama ta rasu‘’ Kawai ji tayi tana fad'ar Innalillahi wainna ilaihir raji'un da k'arfi wanda sai da d'akin gaba d'aya ya amsa, kafin ta sauke idonta kan gadon da Maman take an lullub'eta gaba d'aya har fuskarta.... 200 ne kacal katin waya 300 ga masu buk'ata zasu turo ta wannan accaunt in. 0567838462 FADILA SHU'AIBU NABABA GT BANK In katin wayane ki turo ta wannan number 09037093702, shaidar ki ta biya ma ki turo cikinta Duk wacce za ta sayi littafina ta sayeshi da sharad'in in na mutu ban k'arasa ba ta yafe mini da rai da rayuwa duk a hannun Allah suke, bani da tabbacin zan kai lokacin sai dai muna fatan fin hakanma, Allah kasa mu cika da imani amin. #NWA #KTG [4/26, 8:42 PM] Rabi: BEBE'ARTH Wattpad@Rashuna KATANGA... ...............15 Wani rugugi da hargagi take ji a cikin kwanyarta kafin ta runtse idanuwanta tana karanto dukkanin addu'ar dake bakinta, a hankali taji 'yar nutsuwa na shigarta ta mik'e daga zaman borin da tayi tana rarrashin Nusrat tayi shiru, kafin ta tashi ta fara cuku cukun karb'ar gawar, bayan ta kira Baba ta sanar masa ga sunan zuwa taje ta taro mai taxi, da mai taxi din da wasu samari ne suka taimaka aka sanya gawar cikin motar. Mutane dank'am suka tarar a k'ofar gidansu, mutuwar ta riga ta gama fasuwa. Babane da kansa ya yiwa Mama wanka ya had'ata, ya kirawo su Nusrat suyi mata addu'a, Yusra kuka kawai take yayin da Nusrat ta rintse idanuwanta tana mata addu'a da zazzak'ar muryarta da ta cika gidan gaba d'aya kafin tace da Yusra. ‘’Mama ba ta cancanci zubar hawayenki a yanzu ba, ki rakata da addu'a shi tafi buk'ata.‘’ Share hawayenta tayi ta fara yiwa Mama addu'ar a ranta tana ganin k'arfin halin Yayar tasu ko tace k'arfin imani da tawakkali. Sai da akayi sallar magariba saboda ta riga ta kawo kai kana a kazo fitar da Mama gidan rud'ewa yayi gaba d'aya ana binta da addu'a masu had'awa da kuka suna yi, Yusra kuwa guri ta samu tana kuka da birgima tana fad'in ‘’Kada ki tafi ki barmu Mama, ki dawo garemu dan Allah.‘’ Sai a wannan lokaci Nusrat taji idonta ya fara ruwa, abinda take buk'ata kenan ko za taji sanyin abinda ya dunk'ule mata a zuciya da tsakiyar kwanyarta, janyo Yusran tayi ta rungume tana bubbuga bayanta. ‘’Yayarmu yanzu Mama ta tafi ta barmu?‘’ ‘’To ya zamuyi, dole muyi hak'uri mu karb'i k'addarar da tazo mana a haka, Allahn da yafimu k'aunarta shi ya karb'eta mutuwa tayi mana Katanga da ita, sai dai mu bi bayanta da addu'a shikad'ai ne abinda zamui mata gata da shi, sai dai kuka ya zama dole, dole ne muyi kuka, kukan rashi rashi mafi girma a garemu, amman na kasa ko da d'igar da hawaye, gara na zubar da hawayen Yusra akan azabar da nake sha cikin kwanya da zuciyata.‘’ Har aka share zaman makokin Mama Nusrat na fama da zazzafan zazzab'i da ciwon b'arin kai d'aya, gaba d'aya ta fige ta fita hayyacinta donma Baba yana mata rubutu na kariya da dangana to shine samun d'an lafiyarta, amman da duk ta tayarwa da Yusra hankali don itace me jinyar tata sai Baba idan ya dawo ya lek'osu ko ya kawo mata rubutu ta sha. A hankali suka fara sabo da rashin Mama da rayuwarsu su biyu a cikin d'aki sai Baba idan ya dawo daga kasuwa ya lek'osu, idan ya samu ciniki a kasuwar yakan taho musu da gurasa da nama don idan ba'ai girki a gidan ba wuni suke ba su ci ba babu ruwan wani da su, Nusrat gani tayi rayuwa ba za ta b'ille da su a haka ba in ba so suke su kashe kansu da yunwa ba, don yanzu k'irjinta ciwo yake mata alamun ulcer inta na gab da tashi, gurin Maman Ameema taje ta rok'eta akan tayiwa Baffa Shamsu magana akan ya bata 5000 za ta ja jari (Don yanzu ko Iya ce take da buk'ata sai ta biyo ta hannunta) To sai Allah ya d'orata a kanta a washe gari tayi kiranta ta bata dubu biyar d'in godiya ta dungai mata har da 'yar k'wallar ta kafin ta nufi kasuwa. Sana'ar wainar Shinkafa ta fara yi da miyar taushe da nama, da me k'uli-k'uli in mutum na buk'ata, ciniki take yi sosai don cika gidan ake da masu siyan waina, idan ba ranar makaranta ba ce Yusra ce ke tayata idan kwa ranar makaranta ce ita kad'ai take yi, a haka rayuwa taci gaba da gangarawa yau fari gobe tsumma, suna samu su rufawa juna asiri da wannan sana'ar wainar da take yi. SHUKHURA Bayan barin Yusra gidan kuka ta dinga yi tana jifa da komai na gidan kamar wacce ta zare ta fita hayyacinta a cikin wannan halin Faruoq ya dawo ya tarar da ita, kamar jira take ya dawo numfashinta ya d'auke gaba d'aya shine ya fita da ita a gigice. Dogon suma tayi wanda ya ibeta tsawon kwana uku ba tare da ta san inda kanta yake ba kafin ta farka, babu wanda yayi gigin gaya mata mutuwar Mama saboda Baba da kansa yayi musu waya ya gaya musu kuma dukkaninsu sunje gaisuwa, sai da ta kwana biyu ta k'ara wartsakewa sosai sannan Mustapha ya d'aukota ya kawota gida a cewarsa bazai iya gaya mata mutuwar Mama ba domin baza ta tab'a iya goge wannan memoryn ba, Baba ne da kanshi ya gaya mata babu abinda tace sai kuka kawai da ta wuni tana yi a d'akin Umma don ko k'ofar d'akinsu ba ta taka ba, suma babu wanda ya nuna ya san tazo Yusra ma mugun haushinta take ji, tana ganin kamar ita ta janyo sanadiyar da suka rasa Mama. Umma buri ya cika, kud'i sosai Shukhura ke sakar mata, duk wani abu da ta yayibo ita take kawowa, Mustapha kuwa ya bawa Saminu jari me kauri yanzu su Nimha ma fantamawarsu suke, Nimha taso yin magana ganin yadda Shukhura ta juyawa su Yayarsu baya amman ta kasa saboda itama sai da ta d'aure mata baki, amman duk da haka ita tana taimakonsu a b'oye, sabulun wanka, na wanki omo 'yan kud'i haka tana bawa Yayar tasu, duk da suma yanzu Alhamdlillah suna samu sosai cikin sana'ar wainar da suke yi, suyi girkinsu, su d'inka suturarsu, su biya kud'in makarantar Yusran su kuma kashe gararin gabansu, Yusra ba ta tab'a bari a ci musu mutumci duk wanda ya tab'a Nusrat sai dai idan ba ta gidan, a haka rayuwa ta dunga tafiya tana gangarawa gashi har yanzu shekara guda da k'asa ta rufewa Mama idanu, a wannan shekara babu ranar banza da za tazo ta fad'i ba tare da sun nemawa Mama rahamar Ubangiji ba, tsakaninsu da Shukhura kuwa har yanzu sai kallo, ko jiya da tazo yiwa Umma da Baba sallama zasu koma kano tana ta laulayin ciki ba tace musu ba suma ba suce mata ba..... 200 ne kacal katin waya 300 ga masu buk'ata zasu turo ta wannan accaunt in. 0567838462 FADILA SHU'AIBU NABABA GT BANK In katin wayane ki turo ta wannan number 09037093702, shaidar ki ta biya ma ki turo cikinta Duk wacce za ta sayi littafina ta sayeshi da sharad'in in na mutu ban k'arasa ba ta yafe mini da rai da rayuwa duk a hannun Allah suke, bani da tabbacin zan kai lokacin sai dai muna fatan fin hakanma, Allah kasa mu cika da imani amin. #NWA #KTG [4/26, 8:42 PM] Rabi: BEBE'ARTH Wattpad@Rashuna ®️NAGARTA WRI.ASOCIATION KATANGA... In baki siya ba ya kamata ki mallaki naki a hannu kar garab'asar ta wuce ki, in na gama free page zaki siyeshi akan 300 ne,kuma in kin siya yanzu zaki samu damar karanta CIN AMANA kyauta, kada ku bari wannan garabasar ta wuceku, kada ku manta akwai abin amfani a ciki. Masu tambayata document in na gama, shi kuma zaku sameshi akan 500kacal. ...............16 Babane zaune a shagonsa ya kunna 'yar tsohuwar redionsa yana saurare, yau tun da ya fito ko biyar baiyi ba kamar wanda akaiwa tofin Allah tsine, ko kuma don kayan nasa sunyi k'asa ne Allah ne dai masani. Wani mutum ne ya taho yana jan k'afa d'aya d'aya k'afar da alamu harbinsa akayi don ga jini nan na d'iga daga saman kafad'arsa ma harbinne, sai da yazo saitin da Baba yake ya ajiye masa wata 'yar k 'aramar camera da 'yar farar takarda, "Ka kula sosai rayuwarka za ta iya shiga had'ari, dukkan bayanan na cikin takaddar, kayi k'ok'ari gurin ganin ka isar mini da sak'ona,don tawa ta k'are bazan tab'a shaa ba, amman zanyi farin ciki muddun a hannu me amana na dank'a sak'ona." Yana kawowa nan yayi saurin juyawa yabi ta gefen shagon nasa, kafin lokacin Baba yayi saurin d'auke abinda ya ajiye masa ya b'oye a aljihunsa, yaci gaba da saurarar redionsa amman zuciyarsa cike take da taraddadin wannan al'amari. Wasu mutane ne suka tsaya daga bakin shagon nasa suna nazarin gurin ganin jini ya d'id'd'iga, daga ganin fuskokinsu ba imani zasui ba, zuciyar Baba sai bugawa take cike da tsoro amman ya maze yana saurarar redionsa wanda ba ya ma fuskantar abinda ake fad'i a ciki, kafin su kuma subi hanyar da ya bi saboda d'igar jinin da ya ankarar da su. Baba cike da tsoro da taraddadi ya huni a wannan rana, gashi bai san ya takaye tsakanin mutumin nan da wayannan mutanen ba, a haka har lokacin tashinsa yayi ya tashi ya nufi gida cike da mugun zulumi. Sai cikin dare ya warware takaddar da ya bashi ga abinda ta k'unsa; "Ina fatan sak'ona ya isa hannun me rik'on amana, wanda zai iya siyar da rayuwarsa kamar yadda na siyar da tawa, na san muddun ka kalli abinda ke cikin camerar nan muddun kana da imani za ka so a hukunta wanda ya aikata hakan, ina so a isarmin da sak'on camerar nan hannun Ibrahim Gogel ko kuma Aashiq Aliyu Gogel, kaf ahalin GOGEL ESTATE mutum biyunnan na aninta sak'ona ya isa garesu." Wata jik'ak'k'iyar zufa Abba ya goge, tashin hankali na bayyyana k'arara akan fuskarsa, to shi da baisan fuskokin wa'yannan mutane biyu ba ta ina zai ganesu? Bashi da me bashi wannan amsar, ko da ya kunna camerar kasa cigaba da kallon abinda ke ciki yayi hankalinsa na mugun tashi, a take shima yaji zai iya salwantar da rayuwarsa muddun wannan sak'o zai isa ga wa'yannan mutane biyu, bayansu bai jin zai iya bawa kowa sai dai in su d'auki ransa, d'aga tabarmar dake shimfid'e a tsakar d'akinsa yayi ya hak'a rami ya zira camerar a ciki had'e da takaddar ya rufe ya mayar, a ranar cike da wannan zulumin ya kwana. Bari yayi sai da aka ibi kusan wata guda da faruwar hakan kana ya nufi GOGEL ESTATE dake GRA, securitin dake bakin gate in a k'alla sun kusan su goma kuma majiya k'arfi, to shin ta ina ma zai tunkari wannan gida yace zai shiga? Ya tabbata sai sun rud'asa da tambayoyin gurin wa yazo, shikwa bai shirya amsoshinsu ba don hakan bai san wata matsala za ta janyo ba, yana gama wannan tunanin kawai ya juya zai bar layin, wata motace tasha gabansa da sauri yayi saurin ja baya yana kiran sunan Allah, kafin wasu mutane su fito daga ciki su dannashi cikin motar suka jata da gudun gaske. Har bayan sallar isha Baba bai dawo gida ba, Nusrat sam ta kasa samun nutsuwa a zuciyarta, haka kawai take jin k'irjinta na ta mugun bugawa hakan yasa ta d'aukar carbi tana jaa, tun tana jin motsin Umma har taji shiru alamun itama ta kwanta, Yusra kuwa dama ta jima da yin bacci saboda yau tashi tayi ba ta jin dad'i, Nusrat ba tayi aune ba sai gani tayi har d'ayan dare tayi babu Baba babu labarinsa abinda bai tab'a yi ba kenan, fita tayi taje bakin k'ofar d'akin Umma ta k'wank'wasa mata. Tsaki taji Umman ta jaa had'e da fad'in. "To nima yau babu abinda na dafa sai kaje gurin shafi da man 'yarka ta baka don itace dolenka, haba da kai zanji ne ko da tshohuwar kwad'ayayyar matar can da komai aka kawo mun idonta yana kai, mtsss." Wani bak'in ciki Nusrat taji ya kawo mata wuya, yanzu ya dace ta gayawa mijinta haka don kawai Allah ya jarabceshi da babu, ta manta duk irin d'awainiyar da yayi a lokacin da yake da shi, kuma rashin mutumcin bai tsaya kansa har da uwar da ta diroshi duniya, duk lalacewar iyaye ai iyaye ne ba'a isa a canja musu suna ba, juyawa kawai tayi ta nufi gurin Iya, k'wank'wasa mata k'ofar tayi kafin taji muryarta tace. "Waye nan?" "Iya nice, cewa nayi kinga Baba shiru har yanzu bai dawo ba." "Ke kinjimu da fi'ilin yarinya, Baban naki k'aramin yaro da zai b'ata ko kuwa? Kika sani ko wata harkar samun kud'ince tazo masa." Haushine ya kuma turnik'e Nusrat, wannan son kud'i irin na kakar tasu ba ta san irinsa ba, ita sam babu wani yare da take ganewa sai yaran kud'i masu shi kawai take mutumtawa take darajawa inkwa baka da shi kai da banza duk d'aya hatta a cikin 'ya'yanta ma, Allah ka rabamu da irin wannan zuciyar amin. Gidan Baffa Shamsu ta nufa tana bubbuga musu gida, inda Allah ya taimaketa basui bacci ba kasancewar Mmn Amima ta fita unguwa ba ta dawo da wuri ba hakanne yasa girki yayi mata dare sai kusan shabiyu ta kammala, to shiyasa bayan sun gama ci suka zauna don abincin ya tsarga musu mai makon sui zaman shiru sai suka kunna tv film in da ake kuma yaja hankalinsu har suke buk'atar ganin k'arshensa to sai kuma suka ji bugu wanda ya tsorata Amima da mmanta, Baffa Shamsu ne kawai bai tsorata ba yazo yana tambayar. "waye?" "Nusrat ce" Ta fad'a da muryarta mai son fashewa da kuka, bud'e gidan yayi yana tambayarta. "Lafiya Nusrat kuwa?" "Babane har yanzu bai dawo ba." Ta fad'a tana mai fashewa da kuka, don haka kawai take jin kamar da akwai abinda ya faru da Baban. "Kuma an kira wayarshi?" "Bani da waya ai." Ta fad'a da shashshek'ar kuka. "Kinga kiyi shiru babu abinda ya faru insha Allah sai alkhairi shigo ciki in kira wayarsa muji." Ya kira yafi sau a k'irga ana sanar masa a kashe take, amman yaki ya gasgata hakan gani yake kamar sharrin network ne, shima kuma sai hankalinsa yayi mugun d'agawa, don haka yacewa Nusrat bari yaje kasuwar tasu ya gano, Nusrat ta mak'ale akan sai ta bishi yace tazo su tafi, yacewa Mmn Amima ta rufe gidan in sun fita.... 200 ne kacal katin waya 300 ga masu buk'ata zasu turo ta wannan accaunt in. 0567838462 FADILA SHU'AIBU NABABA GT BANK In katin wayane ki turo ta wannan number 09037093702, shaidar ki ta biya ma ki turo cikinta Duk wacce za ta sayi littafina ta sayeshi da sharad'in in na mutu ban k'arasa ba ta yafe mini da rai da rayuwa duk a hannun Allah suke, bani da tabbacin zan kai lokacin sai dai muna fatan fin hakanma, Allah kasa mu cika da imani amin. #NWA #KTG [4/26, 8:42 PM] Rabi: BEBE'ARTH Wattpad@Rashuna ®️NAGARTA WRI.ASOCIATION KATANGA... In baki siya ba ya kamata ki mallaki naki a hannu kar garab'asar ta wuce ki, in na gama free page zaki siyeshi akan 300 ne,kuma in kin siya yanzu zaki samu damar karanta CIN AMANA kyauta, kada ku bari wannan garabasar ta wuceku, kada ku manta akwai abin amfani a ciki. Masu tambayata document in na gama, shi kuma zaku sameshi akan 500kacal. ...............17 Ba ko wasu mutanene suka d'auke Baba ba face mutanen da suka biyo wannan mutumin da ya bashi camera, yadda suka ga jinin sosai a bakin shagon Baban hakan yasa suka d'ora masa ayar tambaya, har suka sanarwa da ogansu ma'ana wanda ya sanyasu aikin shi kuma ya basu umarnin bin diddiginsa had'e da d'ora masa ido akan dukkan wani motsi da zaiyi, sun so rabuwa da shi da suka ga an ibi kusan wata baiyi wani motsi ba alamun zatonsu bai tabbata ba, amman sai ogan nasu yace suci gaba da sanya masa ido don akwai mutane masu matuk'ar wayo zai iya yuyuwa don ya b'atar da tunaninsu yayi hakan to sai yau kuma ya kawo kansa don suna ganinsa a bakin estate in suka san me ya kawo shi. Azaba iri iri suka gana masa bayan sun gama bincikeshi ba su samu abinda suke so ba,kuma shi sam ya nuna musu bai san akan abinda suke magana ba don haka ogansu ya basu umarnin su kashe shi kawai ta yadda zargi bazai biyo kansu ba suje su wullar da shi a bakin shagonsa. Wuya suka shak'e masa har sai da suka tabbatar ya daina numfashi kana suka sanyashi a mota suka zo suka wullar da shi anan bakin shagonsa, bayan sahun mutane ya auke gaba aya, to ko da Nusrat da Baffa Shamsu suka zo anan bakin shagon suka tarar da shi a yashe, Baffa Shamsu ya d'aukesa suka nufi hospital da shi Nusrat kuwa sai kuka take don sam ta kasa control in hawayen nata. Kusan asibiti hudu sukaje babu gado sai a Gogel Hospital suka samu aka anshesa nan da nan aka bashi taimakon gaggawa anan suka gano doguwar suma yayi, sai da Nusrat taji wannan bayani na likitoci kana ta samu sanyi a ranta, amman duk da haka k'in bin Baffa Shamsu tayi tace yaje ita za ta k'arasa kwana da Baban, amman don Allah ya lek'a mata Yusra ba dad'i itama take ji ba. Sai da garin Allah ya waye kana Baba ya farka, ya riga ya fidda tsammanin cigaba da rayuwa cikin duniya, ya saddakar a cikin kabari zai bud'i idanuwansa sai gashi ya bud'esu cikin duniya, sai dai bakinsa yayi mishi nauyi, kamar 'yar baiwa yake gani a kwance a k'asa amman baijin zai iya kiran sunanta, d'ankwalinta ta shimfid'a tayi sallar asuba sai a lokacin gwanin iya sata ya saceta ta takure cikin hijabinta. Zuwan su Baffa Shamsu ne ya farkar da ita daga baccin da take kuma ta farka da mugun ciwon kai, akan Baba idonta ya fara sauka, duk sun bi sun zagayeshi kowa da tambayar da yake jefo masa bayan sannun da suke masa shi kwa sai binsu da ido kawai yake, murmushi ne ya sauka akan fuskarta sai taji ciwon kan da ta farka da shi yana raguwa a hankula tashi tayi ta k'arasa gaban gadon tana cewa. "Sannu Baba,bara na kirawo likitan." Jinjina mata kai yayi wanda babu wanda ya samu hakan daga gareshi sai ita kad'ai. "To gwanar iya sai ki dinga nuna kamar kinfi kowa damuwa da shi, duk soyayyar da zaki masa baza dai ta huce wacce ni uwar da na kawo shi duniya nake masa ba, don haka kya iya dakatawa don tuni Shamsu ya tafi kirawo likitan tun da muka fuskanci ba ya magana." Ba ta saurari zancen Iyan ba kawai tayi ficewarta, sauri kawai take zubawa sai ji tayi sunyi karo da mutum zuciyarta ce tayi wani irin harbawa har sai da ta danne k'irjinta tayi baya tana k'ok'arin tsugunawa ta d'aukowa mutumin sandansa da ya fad'i hannunsu ya sauka kai a tare d'agowa tayi tana me kallon fuskarsa yayin da shi kuma ya d'auki sandarsa ba tare da ko d'agowa yayi ya kalleta yayi gaba abinsa, fuskarshi kawai da ta kalla taji gabanta yayi wani mugun fad'uwa, a hankali kuma kyakkyawan murmushi ya bayyana a fuskarta can k'asan zuciyarta kuma taji tana fad'in. "Kai kyakkyawa da shi, kamar yadda sandansa yake mai kyau." Ganin tahowar Baffa Shamsu da likitan yasa ta juya ta koma d'akin har lokacin wani annuri ne ke fita akan fuskarta wanda ita kanta ba ta san dalilin zuwansa ba.(Nikwa nace bare kuma ni, ban sani ba ko masu karatu sun sani?) "Zaiyi magana insha Allahu, yana buk'atar hutu ne sosai, don haka kamata yayi dukkaninku ku koma gida, muna da masu kula da marasa lafiyarmu don haka bama buk'atar d'an jinya ko d'aya, idan da matsala zan kirawo wayarka." Yakai k'arshen maganar yana sauke idonsa akan Baffa Shamsu ma'ana da shi yake kenan yayin da Baffa Shamsun ya jinjina masa kai had'e da cewa duk su tashi su tafi, yayin da Nusrat tayi rau rau da ido za tayi kuka tacewa Baffa Shamsu. "Wallahi duk sauran d'akunan naga da masu jiyya, shine zaice mu mu tafi, duk kulawar da za'a bashi ai ba ta kai wacce zamu ba shi ba." "To ai su ba mu san irin ciwon nasu ba, shi ba kiji yace yana buk'atar hutu ba ?" "Kai ka tsaya ma kana mata bayani me kafiyar tsiya ba a banza ba kika rasa mashin shini ai, naga in zaman jinyar nema nice zan zauna tun da mijina ne, ko kuma a bakacin uwarki zaki zauna tun da naga kishi kike tayata bayan rai." "Me ya kawo maganar nan kuma Mamn Nimha, ku shige dan Allah muje." "Kyaleta Shamsu ta wanke min ita tass, yarinya ta d'auki bak'in hali ta d'orawa ranta, kaga fa yadda ita da Yisra suka d'auki karan tsana suka d'orawa Shukhura don kawai yarinya 'yar albarka tana kula da mu, tafi son ta tare kawai a gindinsu saboda bak'in halin tsiya to ke wa ya hana ki fito da naki mijin." "Allah dai ya kyauta, Iya don Allah ku muje ance ba ya son hayaniya kuma neman tayar da hayaniyar kuke." Babu wanda ya kuma cewa komai suka d'unguma suka fita. "Yayarmu ya jikin Baban, naga kuma dukkaninku kun dawo?" Yusra ce da ke suyar waina ta jefowa Shukhuran wannan tambayar, tashi tayi jikin nata da d'an dama, to ganin an riga an hada komai na wainar miyarma tun jiya da daddare Yayartasun tq hadata to shine take yinta dalilin da yasa ma ba ta bisu asibitin ba kenan ta bari idan wainar ta k'are ta bi bayansu sai kuma gasu sun dawo. "Da sauk'i jikin nasa, eh likatanne yace mu taho wai basa buk'atar 'yan jinya." "To su kuma haka tsarin asibitin nasu yake, ko kwa akanmu suka fara yin hakan?" "Wa ya san musu to Yusra." Tana kawowa nan tai shigewarta d 'aki ziciyarta sam babu dad'i, kallo Yusran ta bita da shi tana jin kamar da akwai wani abu dake damin Yayartasun, sai kwa ga Amima tazo siyan waina kafin layi yazo kanta suna dan taba hira da Yusran sai kwa Yusran cewa tayi. "Nikwa Amima akwai wani abu da ya faru da Yayarmu ne na ganta wani iri?" Aikwa Amima ta kwashe komai ta gayawa Yusran, bak'in ciki yazowa Yusra wuya ta bud'e murya tace. "To dai dad'in abin kowa yasan Katanga akai mana tsakaninmu da 'yar uwarmu saboda tsabar son abin duniya, kuma Allah yana nan ba ya,bacci bazai tab'a barin zalincin da akai mana ya tafi a banza ba, uwarmu kuwa da aka ambato tana kwance a kabarinta mun bar mutum da Allah don shi kadai zai mana maganinsa, miji kuwa ba ta isa ta bawa kanta ba sai ranar da Allah ya kawo mata shi, kuma muna nan da rai da lafiya na tabbata wata rana sai kun shiga inuwar Yayarmu, zuciyarta da ban take ba irin tamu bace ni da Shukhura don wallahi na tabbata Shukhura ta dawo hayyacinta ba za ta tab'a yafe muku ba amman Yayarmu kuwa duk abinda kukai mata ba shi zai hana watarana ta tsamo ku daga rana ta sanyaku cikin inuwarta ba." Daga Iya har Umman duk suna jinta tana ta bambami babu wanda yayi tari alamun yana jinta, don Yura iskokan nata ma sunfi na Shukhura tsaf zuciya za ta jaho ta canja musu kamanni in suka kulata. Bayan sallar azahar Yusra tacewa Yayarsu ta tashi ta rakata gurin Baba itama ta ganshi in yaso sai su dawo, tashi tayi ta shirya don itama hankalinta gaba d'aya yana kan Baban, nik'af inta ta sanya kana suka fito suka rufe d'akinsu suka tafi, ko da sukaje zasu shiga d'akin da Baban yake sai aka hanasu shiga ganin hakan yasa Nusrat ta nufi office in likitan, ta kai hannu za ta b'urd'a handle in k'ofar taji wata kakkausar murya na fad'in. "Wannan allurar kawai zakai masa itace za ta k'arasa shi har lahira." Da sauri ta d'auke hannunta daga kai jikinta yana wani irin rawa, tayi saurin barin gurin a gigice. Dama haka asibitinnan yake kashe mutane suke yi, ko wa kuma zasu kashe?Shine abinda zuciyarta ke ta tambayarta kuma bata da me bata amsa, gaba d'aya nutsuwa ta bar gangar jikinta, Yusra sai tambayarta take meke faruwa amman ce mata take kawai ki bari bana cikin hayycina Yusra. "To kenan baza muga Baban ba." "To dai gashi sun hanamu ganinsa Yusra, ni bansan asibitinn me suke nufi da mu ba wallahi." Takai k'arshen maganar kamar za ta kece da kuka, Yusra kuwa bayan wata nurse ta bi ta had'ata Allah annabi akan ta taimaketa taga mahaifinta, nurs in ta rasa yadda za tayi da Yusra duk ta inda ta b'ullo mata sai ta goce, k'arshe dai wasu kayan ta bata irin wanda nurs in ke sakawa tace ta saka sai ta shiga babu wanda zai hanata, godiya Yusran tayi mata ta karb'a ta saka, kasancewar tana da tsayi da girman jiki babu wanda zaice shekarunta goma sha uku kacal, har tazo ta shige Nusrat ba ta lura ba saboda gaba d'aya hankalinta yana kan office in likitan so take taga shi da waye zasu fito daga ciki. Sun samu labarin Baba bai rasu ba don haka suka shiga binciken wani asibiti aka kaishi daga k'arshe suka gano yana nan gogel hospital, shine ogan nasu yayiwa likitan waya akan kar ya bar kowa nasa yaje inda yake, wannan dalilin ne yasa aka koresu zuwa gida yanzu kuma aka hanasu ganinshi, ogan nasu kuma yazo da kansa gurin likitan saboda kasancewar asibitin a k'ark'ashinsu yake kuma likitan ya saba mishi irin wannan aikin idan buk'atar hakan ta taso, shiyasa suka k'ule cikin office insa suna tattaunawa wanda tsautsayi yasa Nusrat ta jiyowa kunnuwanta abinda ya rikirkitata. Tana nan tsaye suka fito shi da likitan, ta cikin nik'af inta take k'are masa kallo, saurayine kyakkyawa da shi amman yake wannan d'anyen aikin shikwa me yasa, ba dai zai wuce kud'i ba wanda tasan sune zasu saka likitanma ya amshi buk'atarsa, a ranta kawai taji tana adduar Allah yasa kar dai likititan ya amshi buk'atarsa, kai da ma wuya kam don irinsu in baa amshi buk'atarsu ba kashe mutum suke. Yusra ce itama ta taho bayan ta fito daga d'akin da Baba yake, sakin baki tayi tana kallonta yayin da likitan ya nufota yana kiranta "Murja" Da alama sunan wacce ta bata kayan kenan, yayin da k'irjin Yusra ya fara wani irin bugu ta daskare a gurin a tsaye... Nayi k'okari ai, dogon typing yana bani wuya, amman zanyi kokari kullum ina post in banyi ba to kumin uzuri ban samu lokaci bane na gode. 200 ne kacal katin waya 300 ga masu buk'ata zasu turo ta wannan accaunt in. 0567838462 FADILA SHU'AIBU NABABA GT BANK In katin wayane ki turo ta wannan number 09037093702, shaidar ki ta biya ma ki turo cikinta Duk wacce za ta sayi littafina ta sayeshi da sharad'in in na mutu ban k'arasa ba ta yafe mini da rai da rayuwa duk a hannun Allah suke, bani da tabbacin zan kai lokacin sai dai muna fatan fin hakanma, Allah kasa mu cika da imani amin. #NWA #KTG [4/26, 8:42 PM] Rabi: BEBE'ARTH Wattpad@Rashuna ®️NAGARTA WRI.ASOCIATION KATANGA... In baki siya ba ya kamata ki mallaki naki a hannu kar garab'asar ta wuce ki, in na gama free page zaki siyeshi akan 300 ne,kuma in kin siya yanzu zaki samu damar karanta CIN AMANA kyauta, kada ku bari wannan garabasar ta wuceku, kada ku manta akwai abin amfani a ciki. Masu tambayata document in na gama, shi kuma zaku sameshi akan 500kacal. ...............18’ "Likita" Nusrat ta fad'i haka tana shan gabansa wanda hakan ya bawa Yusra damar bacewa daga gurin kamar walk'iya. "So muke a sallamemu." Ta fad'i hakan tana d'age nik'af in fuskarta domin ya shaidata. "In lokacin sallamar yayi ai zan sallameku ba sai kun bukaci hakan ba." "To ai asibitin naku ne yayi tsauri da yawa ance babu masu jinya sannan kuma yanzu an hanamu shiga muga mahaifinmu, ai abin baiyi tsari ba sam wallahi." "Ke yarinya ce baza ki gane abinda muke nufi ba, amman zamuyi magana da d'aya namijin." Ya fad'i haka yana neman barin gurin yayin da Nusrat tayi saurin shan gabansa. "Nifa bazan bar asibitin nan ba sai naga mahaifina wallahi." "K'warai kuwa Yayarmu, mu da mahaifinmu ai mana k'arfa k'arfan hanamu ganinsa, bayan duk ga sauran d'akunan marasa lafiyan ana ta shige da fice sai mu za'a hana shiga." Cewar Yusra da ta nufo gurin da suke a tsaye. "Mahaifinku yana buk'atar hutawa sosai, wannan dalilinne yasa muka hana kowa ganinshi, da wani yare kuke so nai muku ku fahimta ne?" "Toh munji, amman yanzu muje tare muganshi sannan sai mu tafi." Suka fad'i hakan a kusan tare, ganin dai babu yadda zaiyi da su don Yusra har gefen rigarsa ta rik'e yace. "To sakeni ku muje d'akin" A ransa yana addu'ar Allah yasa Aasad yayi abinda zaiyi ya fita to sai kuma suna karya kwana suka ci karo da shi, don haka likitan yace su jirashi anan bara yaje ya daho, bai jira me zasu ce ba yabi bayan Aasad in. Cikin muryar tashin hankali Aasad in yace. "Likita akwai matsala" "Bai mutu bane ko wanine ya ganka?" "To ai in wani ne ma ya ganni da sauki don akwai hanyar da zan bi na aikashi lahira shima, ya gudu, baya cikin d'akin na duba ko ina da ina kaga takardar da ya bari akan gado" INA NAN DAWOWA Innalillahi likitan ya hau ambata bayan ya gama karanta takardar. "Yanzu meye mafita, me zan cewa wa'yannan yaran su fahimta" Ya zauna dab'as akan kujera yana jujjuya kansa ya rasa mafita guda d'aya gareshi. "Kai ta abinda zaka cewa iyalinsa kake, ni kuma ta abinda zaije ya daho nake, don haka nayi alkawarin sai na binciko inda ya shiga a duk fad'in garin nan in kwa bai wasa ba sai na kashe dukkanin ahalinsa." Yana kawowa nan ya fice daga ofis in yana banko k'ofar da k'arfi ta bada k'ara mai sauti, likita dai kulle kansa yayi a ciki don in ya fita baisan me zai gayawa wayancen yaran ba don ya tabbata sai sun tara masa mutane, musamman wacce ta rik'e gefen rigarsa don yaga alamun rigimammiya ce, su kuwa da suka gaji da tsaiwa sai Yusra cewa tayi. "Yayarmu zo mu tafi ina jin dai likitannan wayo yayi mana ya gudu, tunda dai na samu na shiga na ganshi ai shikenan." "Wai kayan wa kika saka ne?" "Wallahi wata nurs ce ta bani, ina zuwa kuwa ba tambayar wani d'aki zan shiga tun da sun ganni da uniform, amman dai har yanzu ba ya magana yasa na mik'o masa biro da takarda da aka ajiye kan drowa yayi rubutu a jiki ya bani na baki." Takai k'arshen maganar tana mik'o mata takaddar, karb'a tayi tana fad'ii. "Mu tafi gidan, amman wallahi gobe duk bura'ubar da za'ayi sai dai ayi sai naga Babana." Jinjina kai Yusra tayi, tunda suke bata tab'a jin Yayarsu tayi zagi ba sai yau, soyayyar Baba da Yayarsu daga Allah ne, sun kwana da sanin yafi k'aunarta a cikinsu kamar yadda Mama tafi k'aunar Shukhura sai dai b'oyewa da suke k'ok'arin yi. Likita ya shiga mugun cakwakiya ya rasa yadda zaiyi, taya zaai ace paitent a cikin asibitin nan ya gudu?Dole sai 'yan uwansa sun tuhumesu kuma hakan zai tab'a kimar asibitin wanda ya tabbata Aashiq yaji bazai tab'a k'alewa ba kuma tabbas hakan zai iya sawa ya binciko abubuwa masu yawa da suka bunnesu, don haka kawai ya yanke shawarar zuwa mutuware, ya samo gawar da ba'a gane fuskarta kana yaje yayi report wa 'yan sanda bayan suma ya basu cin hanci me tsoka kana washe gari ya kirawo Baffa Shamsu akan yazo asibiti akwai matsala. Tunda Amima ta shigo ta gaya musu cewar Baffa Shamsu ya tafi asibiti an kitashi akan akwai matsala Nusrat take zabga uwar gudawa mai azaba ta tashin hankali, gaba d'aya gidan kowa ba ya cikin nutsuwarsa,can bayan jimawa da tafiyarsa suka ji hayaniya ar mutane a waje, Nusrat ce ta zabura ta mik'e had'e da fad'in. "Shi kenan sun kashe shi wallahi." Dai dai nan Baffa Shamsu ya shigo, fuskarsa kawai ta kalla ta saki murmushin rashin mafita had'e da fad'in. "Kun gani dama na fad'a wallahi sun kashe mini Babana." Iya da Umma Baffa Shamsu yaja gefe yana gaya musu abinda ya faru k'asa k'asa. "A yadda likitan da police sukamin bayani wai fitowa yayi da niyar guduwa daga asibitin shine su kuma suka bi bayansa a k'ok'arinsa na tsallaka titi mota tabi ta kansa,kuma sunce har yau basu gano dalilinsa na yunkurin guduwa ba, ga gawarsa can na shiga da ita can gida zan had'ata." A tare Iya da Umma suka saki salati da gunjin kuka, hakan yasa Nusrat da ke ta k'ok'arin k'wacewa daga rik'on da Mman Amima tayi mata na sai taje gurin da su Iya suke magana, fasuwar kukansu yasa ta samu amsar da take son zuwa juyowa, a hankali idanuwanta suka k'afe k'af numfashinta ya d'auke gaba d'aya." A hankali idanuwanta suke washewa yana dad'e tariyo abinda ya sameta, cak idonta ya sauka jikin drowar dake gefen gadon da take a kwance, GOGEL HOSPITAL shine abinda ta gani a rubuce, firgicewa tayi hade da zabura ta mik'e tsaye tana me saukowa daga kan gado ta nufi hanyar waje, Sai a lokacin Mamn Amima da Yusra dake tare da ita suka lura suka biyo bayanta a hanzarce. Sauri kawai take zubawa burinta ta fice daga cikin asibitin ba tare da wani ya dakatar da ita ba, karo kawai taji tayi da mutum, wanda shi kuma hakan yasa sandan dake rik'e a hannunsa fad'uwa sukayi baya kamar zasu kifa yaransa dake bayansa suka yo kansa yayi saurin dakatar da su da hannunsa ya rik'eta sosai yana me daidaita tsayuwarsa, ruk'unk'umeshi tayi tana sakin kukan dake cinta had'e da fad'in. "Dan Allah na rok'eka ka fitar da ni daga cikin asibitinnan kashe mutane suke yi sun kashe mahaifina shine nima aka kawo ni su kashe ni " Dago da kanta yayi yana me sauke lumsassun idanuwansa a kan fuskarta, kallon yadda hawayen ke sauka akan fuskarta suna zirarewa yake don ko d'igon hawaye baya tsayawa saboda santsin fatar da Allah ya huwace mata.... 200 ne kacal katin waya 300 ga masu buk'ata zasu turo ta wannan accaunt in. 0567838462 FADILA SHU'AIBU NABABA GT BANK In katin wayane ki turo ta wannan number 09037093702, shaidar ki ta biya ma ki turo cikinta Duk wacce za ta sayi littafina ta sayeshi da sharad'in in na mutu ban k'arasa ba ta yafe mini da rai da rayuwa duk a hannun Allah suke, bani da tabbacin zan kai lokacin sai dai muna fatan fin hakanma, Allah kasa mu cika da imani amin. #NWA #KTG [4/26, 8:43 PM] Rabi: BEBE'ARTH Wattpad@Rashuna ®️NAGARTA WRI.ASOCIATION KATANGA... In baki siya ba ya kamata ki mallaki naki a hannu kar garab'asar ta wuce ki, in na gama free page zaki siyeshi akan 300 ne,kuma in kin siya yanzu zaki samu damar karanta CIN AMANA kyauta, kada ku bari wannan garabasar ta wuceku, kada ku manta akwai abin amfani a ciki. Masu tambayata document in na gama, shi kuma zaku sameshi akan 500kacal. ...............19 A dai-dai lokacin su Yusra suka k'araso, saurin janyota tayi had'e da kallon mutumin tace. "Yi hak'uri don Allah, mahaifinmu ne ya rasu a rud'e take gaba d'aya." Lumshe idanuwansa yayi kawai had'e da amsa sandansa a hannun d'aya daga cikin yaransa da ya tsuguna ya auko masa daga haka yayi gaba abinsa. "Nifa wallahi bazan koma cikin asibitin nan nima su kashe ni a banza ba, bani da k'arfin yin shariah da su amma insha Allah hakkin ran mahaifinmu sai ya tab'a kaf wani me motsi a cikin ahalin GOGEL." Wata muguwar tsawa yaransa da basui nisa ba suka daka mata zasu juyo shima ya daka musu tashi tsawar, k'wafa kawai sukayi suna harararta kana sukai gaba, Mmn Amima tace. "Bata hijabin ta saka mubar asibitin nan tun kan ta b'allo mana ruwan da baza mu iya toshewa ba, tun da mun samu ta farfad'o su rike takaddar sallamarsu." "To haka kawai a daki mutum a hanasa kuka, ai bazai yuhu ba wallahi, daga yau ko akuya naga wani zai kaho asibitin nan sai na hanashi don wallahi asibitin k'arasani ne ba wani gogel hospital." "Munji to, anshi hijabin ki saka mu tafi, ni bansan yaushe kika zama rigimammiya ba wallahi." Hijabin ta ansa ta saka ba tare da ta kuma cewa komai ba tayi gaba. Da Hidaya ta fara yin tozali kafin Nimha ta hangota ta taho da gudu suka rungume juna suka zube a gurin had'e da fashewa da wani irin kuka,Yusra ma bin sahunsu tayi suka had'a kawuna suna sharb'ar kuka, Aunty Maryam ce duk tazo ta d'ad'd'agasu tana basu baki kallon Aunty Maryam Nusrat tayi da jajayen idanuwanta da suka kumbura tace. "An kaishi ne?" "Wani irin an kaishi, abinda har ya kwana a gidansa na gaskiya, don Allah ki daina wannan kukan kinga ko kad'an baki samu damar yi masa addua ba kuma addua yafi buk'ata ba kuka ba kinji ko?" D'aga mata kai tayi a ranta tana mamakin kwana tayi kenan ba tare da tasan inda kanta yake ba kafin idanuwansu su gauraya da na Shukhura tana kusa da Umma duk da carbuna a hannunsu, kautar da idanuwanta tayi ta nufi cikin d'akinsu. Ana share makokin Baba Aunty Maryam tace da Nusrat ta had'a kayanta da ita zata tafi, tayi hakanne saboda Nusrat in ta dinga taimaka mata da girki ga azumin watan Ramadan nan ma ya taho, saboda Aunty Maryam irin mutanen nan ne da suka k'i jinin girki gaba d'aya gashi Abban Hidaya ya tsani cin abincin waje ko na masu aiki, saboda sanin halinta da yayi yasan wataran za ta iya bawa 'yan aikin suyi masa ya kwa yi mata Allah ya isa duk ranar da ta sake ta bashi abincin 'yan aiki yaci, to wannan dalilin ne yasa bata rabo da wamars masu mugun rik'on zafi idan tayi girki tun rana to dashi zasui dinner, kuma duk abincin da take sassauk'a ne, Hidaya me d'an kama mata wani abin makaranta yanzu take zuwa wani zubin sai shida take shigowa, Hibba kuwa in ta bata girki sai yace jagwalgwalo, to wannan dalilin ne yasa tace zata tafi da Nusrat in, don tun rasuwar Mama ma taso tafiya da ita, Hidaya tace tayi mata tayin hakan ta nuna bata so, yanzun ma kuwa Nusrat in rufe ido tayi tace baza ta bi Aunty Maryam ba, idan ta bita ta bar Yusra a hannun wa, Iya kuwa tace dole sai taje, ai su ba mutane bane da za tace a hannun wa za ta bar Yusran, yayin da itama Nusrat ta kafe kan ba inda zata matsa ta bar Yusra, sai dai in tare da Yusran zasu tafi, don wallahi in ta tafi ta barta ta kwana da sanin babu me lura da lamarinta, yunwa tayi sanadiyar rugujewar rayuwarta tunda yanzu sun riga sun zama marayu gaba da baya, to ana cikin hakane Iliya dake a cikin gida,(Ainihin gidan da aka haifi Mama, idan masu karatu basu manta ba)yazo akan a bashi rik'on Yusra yana so, kasancewar matarsa yanzu ma za tayi haihuwar fari tsohon ciki gareta, kuma yana da k'okari gurin zumunci, to ganin babu ran uwa ba uba yasa yace bara yazo ko zaa bashi rik'on Yusra ya samu ladan marainiya, kuma da yaddar matarsa yazo kasancewar kar a samu matsala tunda shi ba zaman gida zaiyi ba tare zai barsu, babu wani ja Iya tace Yusra ta had'o kayanta ta bishi, sanin Iliya yana da mugun kirki da zumunci yasa hankalin Nusrat kwanciya ta taya Yusran had'a duk wani kaya nata dake d'akin, bayan sun rungume juna sunci kukansu sun k'oshi kamar wayanda zasu rabu har abada, kana Nusrat in tayi mata nasiha sosai akan ta kula da rayuwarta ta dinga tunawa su marayu ne basu da uwa basu da uba, har bakin motar Iliya ta rakata, anan d'inma kamar ba zasu rabu ba, dukkaninsu hawaye suke zubarwa suna mugun jin rabuwar tasu a cikin zuciyoyinsu, Iliya ne ya dinga basu hak'uri yana tausarsu yayiwa Nusrat in alk'awarin kula da rayuwar Yusran, ita kuma ta buk'aci ya rubuta mata numbersa a memo, ya rubuta mata kana yaja motar suka tafi, kasancewar shi ba a nan cikin gidan yake a zaune da matarsa ba. A sanyaye ta koma cikin gidan tana jin duniyar gaba d'aya tayi mata fad'i kamar ita kad'ai ta rage a cikinta, duk katangun da suka zagayera sun rushe gaba d'aya, a haka dai ta samu ta gama had'a kayanta tsaf saboda Aunty Maryam ta sanar da ita driver yana hanya, ita Hidaya tun ranar uku ta tafi kasanwar zasu fara zana paper. Ko wata kusuruwa ta d'akin nasu take bi da kallo tana tuno rayuwar da suka dinga gudanarwa a cikinsa tun daga yarinta har zuwa sanda suka mallaki hankalinsu, da yadda suka tashi da ginanniyar soyayyar junansu a zuk'atansu wacce mahaifiyarsu me kyakkyawar zuciya ta gina musu, sai gashi yau an wayi gari tsakaninsu da Shukhura sai kallo, mahaifiyarsu ta tafi ta barsu gashi a yau zasuyi nida da Yusra, taya za ta iya runtsawa a yau babu Yusra babu Shukhura a gefenta? Ta jefowa zuciyarta wannan tambayar yayin da idanuwanta ya sauka akan makwancin nasu, wani irin kuka ta fashe da shi wanda yake tahowa tun daga k'asan zuciyarta, kafin can ta tuna da takaddar da Baba yace Yusra ta bata, duk da ta karanta amman ba tayi abinda ya umarceta ba, ga abinda takaddar ta k'unsa." " Daga gefen hagu na d'akina ki d'aga tabarma zakiga shatar wani guri an hak'a ki hak'a kiciro abinda yake ciki ki ajiye mini, kada ki kuskura wani yasan da zamansa a gurinki ki ajiye mini, ina nan zan dawo." Ashe ba za ka daho ba Baba ta fad'i hakan da dashshshiyar muryarta kafin wani azababben kuka,ya taho mata tana rik'e cikinta da k'irjinta da suke mata mugun zafi, sai da kukan ya tsagaita mata kana ta tafi dakin Baban ta d'auko ba tayi gigin budawa taga ko meye ba ta k'ulle a bak'ar leda tana adana shi cikin kayanta, a lokacin Aunty Maryam tace ta fara fito da kayanta ga direba yazo, k'arfe uku dai dai motarsu ta d'auki hanya zuwa kano, kano ta dabo tumbin giwa ko da me kazo an fika. (To dai Iya da Umma ga gida nan an bar muku ku kadai kuci abinda kuke so kuyi abinda kuka ga dama, Nusrat kuma ko wacce iriyar rayuwa zaai a kano, Iya dama tace mijin kano kike hange shiyasa kika ki tsayar da miji) 200 ne kacal katin waya 300 ga masu buk'ata zasu turo ta wannan accaunt in. 0567838462 FADILA SHU'AIBU NABABA GT BANK In katin wayane ki turo ta wannan number 09037093702, shaidar ki ta biya ma ki turo cikinta Duk wacce za ta sayi littafina ta sayeshi da sharad'in in na mutu ban k'arasa ba ta yafe mini da rai da rayuwa duk a hannun Allah suke, bani da tabbacin zan kai lokacin sai dai muna fatan fin hakanma, Allah kasa mu cika da imani amin. #NWA #KTG [4/26, 8:43 PM] Rabi: BEBE'ARTH Wattpad@Rashuna ®️NAGARTA WRI.ASOCIATION KATANGA... In baki siya ba ya kamata ki mallaki naki a hannu kar garab'asar ta wuce ki, in na gama free page zaki siyeshi akan 300 ne,kuma in kin siya yanzu zaki samu damar karanta CIN AMANA kyauta, kada ku bari wannan garabasar ta wuceku, kada ku manta akwai abin amfani a ciki. Masu tambayata document in na gama, shi kuma zaku sameshi akan 500kacal. ...............20 Biyar da rabi dai-dai suka isa kano unguwar Naibawa, Nusrat sai kallon unguwar take yadda duk ta bi ta canja mata a 'yan shekarun da ta iba ba tazo ba, duk da dai ta jima sosai don tunkan ta bar secondary rabonta da zuwa hutu, unguwa ce ta masu hannu da shuni gidaje ne ga sunan wannan yana wane wannan, gidan Aunty Maryam inma an gyare shi sosai da sosai ba kamar yadda ta sanshi a baya ba da alamu kud'i sun kuma ninkuwa kenan. A cikin jerin d'akunan dake k'asa Aunty Maryam in tace Nusrat ta shiga ciki da kayanta da Driver ya shigo da su, tana shiga toilet kawai ta fad'a ta d'auro auwala a gaggauce saboda la'asar d'in da basu samu sunyi ba bcs a hanya ta riskesu, abin sallah ta shimfid'a kana ta kalli gabas had'e da tattara dukkanin wata nutsuwa tata. Bayan ta idar da sallar ta hau k'arewa d'akin kallo, tsaf yake baya buk'atar gyaran komai sai d'an abinda ba'a rasa ba, bcs kullum masu gyara falon sai sun gyara har da d'akunan da babu kowa a ciki saboda wani zubin mutan gidan sukan amfani da shi da kuma gudun yin bak'o katsaham, tana shirin kishingid'ewa kenan saboda kwankwasonta da ya d'an rik'e sakamakon zaman motar da tayi, tunda yau sha rabonta da yin doguwar tafiya irin haka, dama dai doguwar tafiyar tata iya kacinta kano ba dad'i ba ragi,kuma gashi dama Nusrat in ba gwanar zama bace, haka kawai dai ba abinda take a ganta a zaune gaskiya kam da wuya, muryar Aunty Maryam ce ta katseta daga kishingid'ar da taso yi sakamakon k'walla kiran sunanta da tayi, amsawa tayi had'e da mayar da hijabinta da ta cire ta fita. A tsaye ta tarar da ita tana jiran fitowar tata, don haka tana fitowa ta kalleta had'e da fad'in. ‘‘Yauwa cewa nayi ki d'an shiga kitchen ki sama mana abinda zamui dinner da shi, Hibba kuje ki nuna mata inda komai yake, zanje na watsa ruwa ne.‘’ ‘’Ok Mom‘’ Hibba dake kwance a kushin tana kallo, don Hibba mayyar kallo ce, ta amsa mata da hakan, kallon Nusrat in tayi tace. ‘’Muje Yayarmu‘’ Jalof in taliya tayi wacce tasha su piece, grean beans,carrot, da kuma sadin, sai zuba k'amshi take saboda spices in da tayi amfani da shi, da taurinta sosai da kuma ruwanta ta juyeta a cikin wata k'atuwar warmas, bcs kan azo ci zata k'arasa dahuwa a ciki, idan kwa ta barta ta dahu to zata k'ara dafewa ne kan azo ci, tana cikin had'a cole slow Hibba ta shigo kicthen in tace. "Mom tace, ki had'a juice ta manta ba ta gaya miki ba, mu kinsan gidannan ba ma cin abinci sai da juice gashi kuma dukkaninmu ba ma shan me gas, Aunty Hidaya ce kad'ai me sha, itama kuma coc kad'ai take sha shiyasa Dad yake ajiyewa saboda ita, shi kuma saboda ulcer insa ne ya daina sha, don a gurinsa Aunty Hidaya ta koyi shan coc, amman tunda ulcer taci k'arfinsa ya hak'ura." "Yanzu duk wannan bayanin Aunty Maryam d'in tace kizo kimin?" Dariya tayi had'e da girgiza mata kai, kafin tace. "Nice dai kawai na baki labari, yauwa na ma manta karfa kiyi wanke-wanke muna da me wanke-wanke." Tana kawowa nan ta juya da gudu tunawa da tayi ana ta huceta a film in da take kalla a tashar tauraruwa, Nusrat kuwa a ranta tace dama bata da niyar yin wani wanke-wanke don a rayuwarta abinda tafi tsana kenan ta gwammace ta huni tana girki akan tayi wanke-wanke sau d'aya, don da basu da me wanke-wanken kuwa sai dai Hibba tayi don ba ta jin za tayi, sai dai kuma idan Aunty Maryam ince tace tayi shine za tayi don ba yadda za tayi. Tana gama had'a coleslow in ta had'a ginger juice kana ta jere su akan dining had'e da dukkan abinda za'a buk'ata kana ta shige d'akinta a lokacin an jima da kiran sallar magariba, wanka tayi da ruwa mai zafi sosai had'e da d'auro alwala ta gabatar da sallarta ta magariba, kana ta zauna jan carbi, jin an murda k'ofar zaa shigo yasata d'ora idanta akai don ganin me shigowar, Hidaya ce, da gudunta ta taho ta rungumeta. "Amma naji dad'in zuwanki Yayarmu sosai da sosai, sam Momy bata gayan tare zaku taho ba, yanzunma shigowata kenan Hibba take gayan." Murmushi Nusrat in tayi had'e da fad'in. ‘’Har haka kuke kaiwa a makaratar baku dawo ba?" "Kedai bari, wataranma ina huce haka, donma yau babu cushewar ababan hawa sosai, muna da nisane tsakaninmu da Buk d'in, kuma Exxam in yau ta cajan kai sai shida na fito, yanzun ma a gajiye na dawo likis wanka kawai nake bukata sai Hibba tace min dake aka taho." "Sannunki to kije in kika huta ma had'u, tunda dai burinki ya cika an taho da ni." Dariya Hidayan tayi kafin tace. "To ke me kike anan ne? Dakin baki ne fa." "Aunty Maryam ce tace na shigo nan d'in ai." "Kinji Momy da wani zance, babu fa kowa a k'asan sai su Abdul da Abbas mu duk muna sama, d'ebo kayanki mu koma d'akina." Wani mugun sanyi Nusrat in taji a ranta, don tun d'azu take tunanin yadda zata kwana ita kad'ai a cikin wannan d'akin, amman kuma duk da haka sai ta kalli Hidayan tace. "Kidai fara gayawa Aunty Maryam in muji me zata ce." Tsaki Hidayan taja had'e da d'aukan d'aya daga cikin jakar katan Nusrat in tayi gaba tana fad'in. "Malama ki taso, nasan zaki takura idan kika kwana ke kad'ai a cikin d'akin nan, kin manta idan kika zo a cikin d'akina kike sauka, wannan ma bansan dalilin da yasa Momyn tace ki shigo nan d'in ba." "To ai wancan zuwa nayi na tafi, wannan kuwa zuwa ne na bansan ranar tafiyata ba." Hidaya dai tayi gaba don bai zama lallai taji me tace ba, Hibba tacewa ta biyota da jakarta da littattafan da ta watsar akan kushin ta haye staires da jakar kayan Nusrat in, sai da ta fara shiga d'akinta ta ajiye kana ta nufi d'akin Mom in tasu, akan sallaya ta tarar da ota da alamu jira take a kira sallar isha ta gabatar da ita kana ta shirya tarbar Dad insu don ga komai nata nan ta fito da shi ta dora a gefen gado. "Momy Sannunku da dawowa, ya hanya?" "Yauwa Hidaya, sai yanzu, ya paper?" "Alhmdlillh Mom, ashe tare kuka taho da Yayarmu?" "Eh saboda girki na taho da ita, ga azumi yana tahowa ." "To amma Mom me yasa kika ce ta zauna a d'akin k'asa?" "To wani d'aki kike so na bata, kinsan dai babu wani daki da ya rage a samannan idan kuma ba ni kike so na fita ba bata nawa ba." "Wa Ni na isa?cewa nayi ta dawo dakina, kinsan ba ta saba kwana ita kad'ai ba." "Babu matsala, tunda kinga zaki iya hakan, ni bara nayi sallah." Takai k'arshen maganar tana k'ok'arin mik'ewa jin hakan yasa Hidaya tashi ta fita daga dakin.. #NWA #KTG [4/26, 8:43 PM] Rabi: BEBE'ARTH Wattpad@Rashuna ®️NAGARTA WRI.ASOCIATION KATANGA... In baki siya ba ya kamata ki mallaki naki a hannu kar garab'asar ta wuce ki, in na gama free page zaki siyeshi akan 300 ne,kuma in kin siya yanzu zaki samu damar karanta CIN AMANA kyauta, kada ku bari wannan garabasar ta wuceku, kada ku manta akwai abin amfani a ciki. Masu tambayata document in na gama, shi kuma zaku sameshi akan 500kacal. ...............21 "Kinsan ban fiya son jalof in taliya ba in ba a lokacin da aka gamata zanci ba." Cewar Dad in Hidaya yayin da Aunty Maryam ke saving insa. "Afuwa nake nema Daddynsu, kasancewar yamma tayi shiyasa nace tayi sassauk'an abu." Hade fuskarsa yayi kafin ya tambayeta. "Waye yayi?" "Nusrat ce" "Wace Nusrat in?" "Nusrat d'in Yaya Audu." "Kai, amma wallahi kin mugun kyautawa, meyasa baki hado da Yusran ba?" "Wallahi nima da har da ita naso tahowa, to d'an uwan mahaifiyarsu ne ya d'auketa." "To ai shi kenan tunda mun samu Nusrat d'in." Daga haka yayi bismillah ya fara cin abincinsa don har ta gama saving nasa ta yiwa kanta, kana Abbas da Abdul kowa ya zuba yadda yake buk'ata, sunyi nisa da fara ci kafin Nusrat da Hidaya su fito, Hidaya ce tayi saving in Nusrat kana taiwa kanta suka fara ci ba tare da ko tari sunyi ba saboda dokar Daddy ce ba'a magana yayin da ake cin abinci. Bayan gama cin abincinsu duk a falo suka yada zango kowa yana ta zuba santin dadin abincin, kasancewar basu taba cin jalof in taliya da taji kayan had'i irin haka ba, hasali ma basu taba cinta da hadin coleslow ba sai yau, Daddy me k'orafin baison jalof in taliya in ba a lokacin zaici ba sai gashi yace gobe ma da ita zasui dinner. Sun gaisa da Nusrat ya k'ara mata ta'aziya, ya kuma ce yaji dad'in tahowa da akayi da ita, zai rik'eta tamkar su Hidaya, shima yana so ta rik'eshi tamkar mahaifinta duk abinda take bukata kar taji nauyin sanar da shi, yayin da ita kuma ta dunga zuba mishi godiya, yana shirin barin falon yace. "Nusrat da fatan kin taho da takaddun makarantarki, da zaman da zaki kawai kema zan nema miki Buk sai ku dinga tafiya da Hidaya?" Wani mugun sanyi ne ya ratsa zuciyar Nusrat, tana da burin yin karatu,kuma bata taba tunanin zata samu cikar wannan burin nata ba cikin sauk'i, sai gashi babu zato babu tsammani burinta na gab da cika, yayin da Aunty Maryam kuma taji k'irjinta yayi mugun bugawa, ita mahaukaciyar ina ce da zata bari ya saka Nusrat in a makaranta, to kenan meye amfanin tajowa da ita, saboda girki ta daukota idan kwa tayi saken da ya sanyata a makaranta to tabbas girki kanta zai dawo babu batun hutun da take hangowa kanta, kuna ita a rayuwarta ba ta k'aunar mijinta ya kashewa wani kud'i idan ba ita da 'yayanta ba, inda Allah ya taimakeshi don a tsaye yake shiyasa yake samu yana hidimtawa yan uwansa, kuma Aunty Maryam ba ta iya bin malamai ba batta da bak'in halinta dai, Nusrat in na k'ok'arin yin magana yayin da Aunty Maryam tayi saurin rigata da cewa. "Ai Dadynsu Nusrat bata da sha'awar yin karatu kwata kwata, tun sanda akayi bikin su Shukhura na samu na lallaba Yaya Audu akan ya bar Nusrat d'in ta fara zuwa ko ABU ce kafin itama Allah ya kawo mata nata mijin,ni zan dauki nauyin karatun nata amman yarinyar nan ta bulan k'asa a ido, ta tirje ita akan baza taci gaba da makaranta ba." Takai k'arshen maganar tana jifan Nusrat in da kallon gargad'i. "Kekuwa Nusrat me yasa ba kya son karatu, karatu da kike gani yana da mugun muhimmanci cikin rayuwar dan adam,kuma shine hasken rayuwarsa, yanzu ma mazan sunfi son mace me ilimi, nidai inai miki sha'awar cigaba da makaranta, idan kin shirya hakan kozo ki sameni." K'asa tayi da kanta don jin yadda k'walla ta ciko mata idanu cikin sanyin murya tace. "Ni da saboda yadda nake jin ana fadin tarbiyar yara na lalacewa shiyasa nak'i yadda, amman insha Allah zanyi tunani na gode." "Hidaya ki wayar mata da kai, duk abinda kuka yanke kuzo ku sameni." Hidaya da bakin cikin Momyn tasu duk yabi ya isheta, don ita a sanin da tayiwa Nusrat tana da mugun son cigaba da karatu don kawai bata samu damar hakan bane, yana daya daga cikin abinda yasa taso Nusrat in ta biyosu bayan mutuwar Mama don ta samu damar cigaba da karatun amma Nusrat in tak'i, wannan labarin k'anzon k'uregen da Momy tayi kuwa ba ta san lokacin da akayi ba, kuma ba ta jin ma anyi hakan, kawai Nusrat in ta karbi hakanne don babu yadda za tayi kuma ta lura da irin kallon da Momyn ta jefeta da shi. "Zan wayar mata da kai kuma zata aminta insha Allah." Tacewa Dadyn nasu da ya fara hayewa samansa Wani shegen kallo Aunty Maryam ta watsawa Hidaya kafin tayi hanyar kitchen hade da cewa Nusrat ta biyota. "Nusrat kar kiga laifina ko d 'aya, na d'aukoki ne dama saboda girki Daddynsu ba ya cin abincin 'yan aiki kuma bai yadda 'yayansa ma suci ba, wannan dalilinne yasa bani da me girki, to shiyasa na d'aukoki, yanzu idan na bari kika fara zuwa makaranta ai banga amfanin tahowa dake na ko kad'an don haka ina umartarki ki cire rai da karatu don bashi na d'aukoki yi ba, ki kuma sanar mishi ke sam ba kya sha'awar cigaba da karatu, kika sake kika bada k'ofar da zaisan ni na hanaki wallahi sai nayi mugun sab'a miki ko da kuma kin koma can zariyan da zama baza ki taba jin dadin zaman can ba don sai na kuma lalata tsakaninku. "Bama zan bada k'ofar hakan ba, zan sanar masa kamar yadda kika ce." "Hakan shine zaman lafiyarki kuwa." Daga haka ta shiga nunnuna mata duk wani abin amfani a kitchen d'in, ta kuma sanar mata daga yanzi ita zata dingai musu Break fast,launchin nd dinner. Hidaya kamar za tayi kuka ta samu Aunty Maryam akan ra bar Nusrat in ta soma makaranta, amman ta rufe ido taiwa Hidayan tatas kuma tace ta sake ta sanarwa Daddynsu ita ta hana sai tai mugun sab'ar mata. Hidaya da Nusrat babu wata hira da suka yi suka kwanta kasancewar zuciyoyinsu babu dad'i kowa da tunanin da yake sak'awa, ita Hidayan kunyar Nusrat inma take ji saboda abinda Mommyn tasu tayi mata, ai ko babu komai Nusrat d'inma d'iyarta ce kamar yadda suke 'ya'yanta, amman son kan Momyn tasu yasa taki fahimtar hakan duk ko k'ok'arin da tayi na fahimtar da ita sai ma rabuwar ba dadi da sukai tsakaninsu. Washe gari tun asuba da ta tashi ba ta koma ba ta sakko k'asa ta had'a break fast ta jeresu akan dining, kana ta koma sama ta kwanta a lokacin Hidaya har ta gama shiryawa, Hibba da Abbas ma haka, Abdul shi ya gama secondary nan da sati aya ma zai tafi chennai acan zaici gaba da karatunsa, Abbas ma saura shekara daya ya gama yana gamawa zai bi bayansa, Hibba kuma wannan shekar zata tafi SSS one tare suke tafiya da Yusra saanni ne ma.... 200 ne kacal katin waya 300 ga masu buk'ata zasu turo ta wannan accaunt in. 0567838462 FADILA SHU'AIBU NABABA GT BANK In katin wayane ki turo ta wannan number 09037093702, shaidar ki ta biya ma ki turo cikinta Duk wacce za ta sayi littafina ta sayeshi da sharad'in in na mutu ban k'arasa ba ta yafe mini da rai da rayuwa duk a hannun Allah suke, bani da tabbacin zan kai lokacin sai dai muna fatan fin hakanma, Allah kasa mu cika da imani amin. #NWA #KTG [4/26, 8:43 PM] Rabi: BEBE'ARTH Wattpad@Rashuna ®️NAGARTA WRI.ASOCIATION KATANGA... In baki siya ba ya kamata ki mallaki naki a hannu kar garab'asar ta wuce ki, in na gama free page zaki siyeshi akan 300 ne,kuma in kin siya yanzu zaki samu damar karanta CIN AMANA kyauta, kada ku bari wannan garabasar ta wuceku, kada ku manta akwai abin amfani a ciki. Masu tambayata document in na gama, shi kuma zaku sameshi akan 500kacal. ...............22 A cikin 'yan kwanakin da Nusrat tayi kowa yana mugun jin dad'in zama da ita, ga kuma girkunan da take musu kala kala wanda da basa samun kamarsa saboda k'iwar Aunty Maryam, shi kanshi Daddynsu yana mugun jin dadin girkin Nusrat in kullum cikin zuba santi yake yana shi mata albarka. Ko a fuska ba ta taba nunawa Aunty Maryam taji zafin hanata makaranta da tayi ba, ta saki hakan a ranta idan Allah ya rubuta za tayi to tabbas ta tabbata hakan zaizo cikin sauk'i, abinda tayi amanna da shi kenan ta saki ranta tana mugun ji da Hibba tana jinta tamkar Yusranta don tana mugun d'ebe mata kewarta, yanzu haka ma tare suke a kitchen za ta d'ora dinner sai Hibba cewa tayi. "Dan Allah Yayarmu kiyi mana macaroni yau duk gidannan." Bata damu da macaroni ba, sam ba ta birgeta a cikin nauikan abinci, kuma a dan zamanta a gidan ta fuskanci suma basu wani damu da ita ba shiyasa ba ta tab'a gigin dafata ba, amman yau da Hibba ta buk'aci hakan sai taji kawai tana sha'awar dafa tan." "Ai ba ma sai kin hadani da Allah ba, yau kowa da macaroni zaiyi dinner." Tsalle Hibba tayi had'e da fad'in. "Yeee Yayarmu shiyasa nake mugun sonki, da me zan kama miki?" Murmushi Nusrat tayi had'e da fad'in. "Nima ina sonki Hibbata." Kafin ta bata abinda zata rage mata da shi. Hidaya ce ta shigo kichen in ta tarar da su suna yanka salak,cabeji da su cocumber suna hira, kasancewar yau da wuri ta dawo daga scl takadda daya suka zana, da dukkan alamu Hidaya Aunty Maryam ta biyo don itama mugun k'uiyya ce da ita ba kamar Hibba ba da bata da son jiki ko kad'an, don ba ta yadda masu aiki su gyara mata dakinta da kanta take gyare abinta sakamakon Hidaya da komai ma 'yan aiki ne suke mata zuwan Nusrat ne itama ta daina bari 'yan aiki suna gyara musu take yi da kanta. "A'a yau wani delecious in ake had'a mana kuma?" Takai k'arshen maganar tana bud'e tukunyar da Nusrat in ta zuba macaroni tana ta tafasowa, yatsina fuska tayi tana kallonsu gaba aya, yayin da Hibba ta k'yalk'yale da dariya. "Haba Yayarmu me yasa zaki biyewa Hibba ki dafa wannan abar, wallahi kaf gidanna babu me sonta hatta Daddy ma, Hibba ce kad'ai don kuma ita kad'ai Daddy yake bari ana had'owa da ita cikin kayan abinci, in tana shaawa sai ta saka a dafa mata." " Yo ni da nake bak'uwa ai ban san da haka ba, yanzu tun da na riga na dafa haka kowa zai hak'ura yaci, nima ba sonta nake ba, amman tunda Hibba na so babu case ko Hibba?" "Haka zancenki yake Yayarmu babu d'igon gyara ko aya." Wata muguwar harara Hidaya ta zabga mata had'e da fad'in. "Ku da Daddy don nikam babu ruwana." Daga haka ta juya ta bar kichen in cike da takaici, don tayi mugun tsanar macaroni gashi wata muguwar yunwa take ji, ulcer inta ce ta motsa da taci abinci za taji tamkar ba ta ci ba. "Ai kar ki damu, idan Daddy yaci wannan girkin na tabbatar miki sai yayi mana babbar kyauta." Cewar Nusrat wanda ba ta tabbatar taji ta ko ba ta ji ta ba. Suna gamawa suka jere komai akan dining kana kowa ya nufi d'aki don jin ana kiran sallar magariba, wanka Nusrat ta fara shiga tayi kana ta d'auro alwala, sai da ta fara gabatar da sallar magariba kafin ta auko vaselin inta ta shafe ko wani loko da sak'o na jikinta, don haka Nusrat take ko ina na jikinta sai ta shafeshi da mai musamman lokacin sanyi ko kad'an ba ta bari fatarta ta bushe ko alwala ta d'aura sai ta kuma shafe jikinta da mai, kallonta Hidaya take tana daga kwance akan gado tana chart, kasancewar hutun sallah take, gyaran murya tayi, wanda hakan yasa Nusrat in ta d'aga kai ta kalleta kafin Hidayan tace. "Yayarmu kinji dad'inki wallahi, fatarki tana da mugun kyau, har wani glowing take,wani rantsewa zaiyi da desighners mayuka kike amfani nan kwa bai san vaselin ne manki ba ainihin fatarki ce da Allah ya baki, kika fara amfani da mayukan gyaran fata ban san kuma ya zaki zama ba ." "Kai Hidaya, kema fa fatarki tana da kyau, ta ma fi tawa shek'i." "Haka dai kika ce, kuma ni ai da taimakon mayukan da nake amfani da su shiyasa, kema so nake mu gama paper nan na anshi kud'i gurin Daddy muje shoppin kina buk'atar abubuwa da dama, kuma nace ki dinga amfani da nawa kink'i." Takai k'arshen maganar tana gallara mata harara, dariya Nusrat in tayi tace. "Sorry, mantawa nake yi wallahi, na riga na saba using da nawa ne." "Hmmmm ke dai kika jiyo, ai jibi zamu zana takaddar k'arshe gata kuwa shoppin zamuje, kan nan naki ma ware shi zaki muje saloon a wanke miki shi sai ai miki stratchine tunda ba kya yin shampoo, kefa Yayarmu ba matar k'ananan mutane bace wallahi, kalarki irin ta hamshak'an masu nairan nanne wanda ake kira young biloniars (mijin novel)shiyasa naso ki fara scl yadda zaki kuma gogewa ki kece raini." Murmushi Nusrat in tayi kafin tace. "Allah dai ya had'amu da mazaje na gari amin." Ta fad'i hakan don kawai ta kautar da maganar schl in da ta jefo. Hibba ta riga kowa zama a dining, sanda duk suka fiffito lokacin a plate na biyu take, Daddy ne yace. "Kaga su Hibba, yau mutuniyar aka dafa miki ne?" "Ai Daddy gaba d'aya gidannan yau aka yita, tayi mugun dad'i wallahi, a plate na biyu ma nake." A dai dai nan Mommy ta bud'e wamars in da macaronin ke ciki a tare duk suka yatsuna fuska yayin da Hidaya ta hurgawa Hibba hrara had'e da fadin. "Ba dole kiji dadinta ba tunda kina sonta, abinda baka so baza ka taba jin dadinsa ba ai." "Sai dai in baiji had'i ba kuwa." Ta fad'i hakan tana dariya k'asa k'asa. Daddy dai cewa Mommy yayi yar kad'an za tayi serving nashi, itama kad'an in ta zuba Hidaya dai cika plate tayi saboda yunwar da take ji zata daure ta cusa haka, kuma da alamu kidney sourc in zata saka macaroni shiga saboda sai zuba k'amshi take, Abdul ma dai to ba laifi wacce ya zuba, kallon Momy Hibba tayi tace. "Mommy ba ki saka muku wannan ba." Takai k'arshen maganar tana nuna American Garden, U.S. Mayonnaise, 'yar tsuka Mom ta ja had'e da fad'in. "Ni ke rabu da ni, macaronin ma sai an mata wani fiili da ban." "To kai Daddy a saka ma wallahi da mugun dadi." Ta fad'i hakan tana mayar da kallonta kan Daddyn. "To saka mini." Yace da ita, da hanzari ta mik'e ta saka mishi,yana yin one sepun ya fara girgida kai yayin da yayi 3 spun kuwa sai cewa yayi. "Wai wata irin macaroni ce wannan?" Hibba na dariya tace. "Daddy doga ce." "Kai amma tana da dad'i wallahi, gobe ma da ita zamui dinner." Dariya Hibba tayi tace. "Dama Daddy na gaya ma macaroni tana da dad'i sai dai in ba ta ji had'i ba, ba kaga su Aunty Hidaya ko magana baai ba ana ta ziri, momy kuwa har k'arawa tayi." Takai k'arshen maganar tana tintsirewa da dariya, Daddy sai cewa Momy yayi nima k'aro mun to, basui aune ba Abdul har ya cinye zai kara, Hidaya kuwa ta kusa tashi da wacce ta zuba don ba k'arya girkin yayi mata mugun dad'i, Nusrat ma tayi mata dad'i sosaia ranta sai mamakin Daddy take watakan shi in girki yayi masa dadi washe gari shi zaa maimaita, bayam kammala cin abincinsu Daddy yace Hibba ta biyoshi ta ansar musu kyautarsu don girkin yau ya mugun kayatar da shi.. 200 ne kacal katin waya 300 ga masu buk'ata zasu turo ta wannan accaunt in. 0567838462 FADILA SHU'AIBU NABABA GT BANK In katin wayane ki turo ta wannan number 09037093702, shaidar ki ta biya ma ki turo cikinta Duk wacce za ta sayi littafina ta sayeshi da sharad'in in na mutu ban k'arasa ba ta yafe mini da rai da rayuwa duk a hannun Allah suke, bani da tabbacin zan kai lokacin sai dai muna fatan fin hakanma, Allah kasa mu cika da imani amin. #NWA #KTG [4/26, 8:43 PM] Rabi: BEBE'ARTH KTG 23 Kamar yadda Hidaya tace a washe garin da suka gama zana paper ta anshi kud'i hannun Daddynsu suka shirya suka fita, saloon suka fara zuwa aka gyara musu kansu da jikinsu da k'afafuwansu, sunyi matuk'ar kyau ainun musamman ma Nusrat in da ba tab'a yi tayi ba wannan ne karonta ba farko sai fuskarta tayi wani irin haske na ban mamamaki wanda ya k'ara fito da zallar kyahunta, daga saloon in sai suka huce shopping mall, Hidaya ce ta dinga jidar mata duk wani abu da ta san tana da buk'atarshi, bayan ta gama ta kalleta tace. "Idan akwai abinda kike so a ranki ban d'auka ba ki d'auka." Murmushi tayi had'e da fad'in. "Ai kin riga kin gama d'aukar duk wani abu da nake da buk'atarsa." Da sukaje b'arin under wears ne kawai ta d'aukarwa Yusra wasu 'yan k'ananun brezia guda biyu, sai pant ma biyu undis biyu,don suna da buk'atarsu dama sosai bibbiyu ne da su sike lanjarawa musamman ma Yusran pant inta duk sun ragargaje dama siya mata pant in yana ranta da kuma brezia don k'irgar dangin nata sun bayyana sosai, kallon breziar da ta d'auka Hidaya take yi kafin tace wani abu Nusrat in ta rigata da fad'in. "Yusra na d'aukarwa." Murmushi kawai Hidayan tayi kafin ta kuma d'aukowa Yusran komai uku suka zama biyar biyar kenan, ko da sukaje gurin biyan kud'i auna kayan nasu kawai akai kana sukace an biya musu da mamaki a fuskokinsu suke tambayar wanda ya biya musu, da hannu suka nuno shi, Nusrat da Hidaya suka juya a tare yana zaune kan kujera ya hard'e k'afafuwansa idanuwansa gaba d'aya suna kan fuskar Nusrat wanda hakan yasa Nusrat in saurin kautar da idonta daga kanshi don tayi mugun tsanar kallo a rayuwarta shiyasa ta d'auko nik'af inta zata saka amman fafur Hidaya ta hanata sakawa, hijabin ma cewa tayi wallahi baza ta saka ba don dole tayi rollin da mayafin doguwar rigar da ta saka wacce Hidayan ce ta bata, sai tayi masifar kyau musamman yanzu da akai musu gyaran jiki da na kai da fuska. Hidaya ce ta k'arasa gurinsa don jin dalilinsa na biya musu wa'yannan mak'udan kud'i don ba k'aramar siyayya sukayi ba, siyayyar da sukaima ina jin lefan wata ne a yanzu. Gaisawa sukayi a mutumce kafin ta amayar masa da tambayar da tazo da ita, duk da ta lura da yadda idanuwansa ke kan Nusrat duk da ta juya musu baya. " Na biya muku kud'ine saboda nauyinku da ya hau kaina a yau yau d'innan, Sunana ISHAQ, k'addarar had'uwata da 'yar uwarki ce ta kawo ni nan, babu k'arya 'yar uwarki ta kama mini zuciya ba kad'an ba nima ina buk'atar a bani damar da zan kamo tata, kuma ina jin da taimakonki ne hakan zai faru ." Murmushi Hidaya tayi tana jin dad'i a ranta, don a kallo d'aya da tayiwa Ishaq ta yaba da shi. "To amma tun kan ka samu shiga shine ka d'orawa kanka wannan d'awainiyar kud'in ai sunyi yawa muma da kudinmu muka zo." Murmushi yayi wanda ya k'ara fito da zallar kyahunsa da k'uriciyarsa a ransa yace, tabbas wannan da ta san waye shi to da ba ta ambaci wannan kud'in da ya biya musu a kud'i ba, ba ta san mall inma gaba aya a k'ark'ashinsu yake ba, amman dai ba yanzu yake son su san shi waye ba sai komai ya dai daita. "Kada ki damu, na riga na gaya miki a yau d'innan nauyinku ya dawo kaina, damar aikata hakan kawai nake buk'ata, da fatan zan samu?" " To bazan ce ba amman zan gwada taimakawa." Wani k'awataccen murmushi ya saki kafin suti exchang in number ya d'ebo rafar 'yan dubu ya bata tak'i amsa, babu yadda baiyi ba amman tak'i amsa don haka ya hak'ura zuwa lokacin kuwa Nusrat ta gaji da tsaiwa ta fice daga gurin, jikin motarsu taje ta jingina tana bin mutanen da suke shiga suna fita da kallo, sai ga Hidayan da Ishaq in sun fito a jere suna hira, tun da suka tunkaro gurin da take a tsaye idanuwansa suke kanta, ta kuma had'e fuakarta guri guda tana k'in kallar gurin da suke tahowa, shikuwa ko wani kallo da yake mata mutuwa yake da soyayyarta da tayi mishi kamun farat daya a kuma kallo d'aya had'uwa d'aya, Hidaya na bud'e motar tayi saurin bud'ewa ta shiga don a takure take da kallonsa, yayin da Hidayan ta bud'e boot ana zuba musu siyayyarsu, yana tsaye yana binta da kallo ba tare da yace mata kanzil ba har aka gama zuba musu kayan sukai sallama da Hidaya taja motar yana tsaye yana karb'ar sabon yanayin dake bak'untar zuciyarsa abinda bai tab'a ji game da wata yarinya ba sai akan Nusrat bazazzagiya. Suna tafe babu wanda ya tofa komai sai can Nusrat ta numfasa tace. "Amman saurayin nan naki ya fiya kallo wallahi." "Saurayina ko saurayinki?" "Saurayinki mana, naga daga zuwa tambayarsa kika shantake kuna shan hira." "In saurayina ne to akan wani dalili zai ta kallonki? Ke yake so, saboda kema ya biya mana wa'yannan kud'in." "Ni kuma?" Ta tambaya had'e da zaro idanuwa." "K'warai kuwa, harma na bashi dama gobe zaizo insha Allah." "Kinyi kuskure Hidaya,na bashi damar da kika yi, zuciyata ta dad'e a rufe saboda alk'awarin da na karb'a har guda biyu, gara d'aya a mafarki ne d'ayan kuma a gaske ne ina kuma son cikashi, kada ki zama silar da zan karya alk'awari don Allah, zuciyata tana da rauni." "Wani alk'awari, wa kuma kikawa?" Sai da ta fara murza zoben azurfar da ya saka mata kafin tace. "Yaa RJ" Ta fad'i hakan tun daga k'asan zuciyarta, wata muguwar faduwar gaba ce ta ziyarci Hidaya wacce ba ta shiryawa ba har ta kusa bugawa wani mai adai daita ba shiri taja wani burki kuuuuuuu kike ji, cike da tsoro Nusrat ta rintse idanuwanta tana salati kafin ta bud'esu akan Hidaya da ta had'a uwar zufa lokaci guda tana k'ok'arin gangarawa gefe tayi parking tana mayar da numfashi. Kenan Yaa RJ son Nusrat yake? Sai yanzu take tuno maganarsu ta rannan da yake tambayarta. "Nikwa Hidaya ina Nusrat?" "Tana nan lafiya, amman ta kwana biyu ba tazo mana ba." "Amman dai ba tayi aure ba ko?" "Eh ba tayi ba, na Shukhura dai akayi." "Alhmdlillh, Alhmdliillh amman naji dad'i sosai." "Yaa RJ cewa nayi ba tayi aure ba fa amman kake ta murna haka." Kawai sai ya basar a zuwan ya zaci cewa tayi duka sunyi aure, da kuma hirar su da take ce masa Nusrat in ta dawo gidansu da zama taga yadda yake nuna farin cikinsa a fili, har ya dunga zumud'in dawowarsa a ranar ma ya sanar mata bayan sallah zai dawo insha Allah." "Hidaya wai lafiya, me ya faru ne?" "Wallahi kaina ne ya fara juyawa Yayarmu, da kin iya jan motar ma ke zaki jamu." "Wayyo sannu, mu d'an tsaya kiji dai dai tukunna." D'aga mata kai kawai tayi tana jingina da kujera ta lumshe idanuwanta tana jin yadda kanta ya fara sarawa a gasken, fuskar Yaa RJ ce take mata yawo a idanuwanta,gaba d'aya zuciyarta ta gama mutuwa a sonsa da k'aunarsa, ya riga ya jima da raunata mata zuciya gaba d'aya ya ya za tayi idan ya tabbata zuciyar RJ Nusrat take so, me hakan yake nufi? To tunda har ya sanyata yi masa alk'awari sonta yake Kenan, da babu soyayya me zai sanya yace tayi mishi irin wanan alkawari me girma? Sai a yanzu duk k'wak'walwarta take tariyo mata yadda yakewa Nusrat in idan tazo gidansu shiysa kenan tun a lokacin Momy take nuna ba ta son alak'ar Nusrat in da RJ? To koma dai meye a yadda take jin soyayyar RJ tana huda ko wani sassa na jikinta ko kad'an ba ta jin za ta iya barwa Nusrat in Rjnta.... [4/26, 8:43 PM] Rabi: BEBE'ARTH KTG 24 Ana sallar magariba suka shiga gida, Momy ta hausu da fad'a musamman Nusrat tunda ta san zata d'ora dinner shine taje ta biyewa Hidayan sukai dare haka, hak'uri ta bata had'e da nufar kichen in don ta d'ora dinner in, a gaggauce tayi musu jalof in couse-couse sai su piece, grean beans,carrot da kidney da ta saka a ciki yayi sha shar da shi sai zuba k'amshin curry da spices yake, mango juice ta had'a ta bar Hibba ta jajjerasu akan dinning ta haye sama don a matse take audigar jikinta duk ta takura mata so take tayi wanka ta canja wata, ga mararta kad'an kad'an tana mata ciwo, yaune dama ta tashi garau amman jiya da shekaran jiya kamar baza tayi ba saboda azababban ciwon mara har sai da aka kira doctor in gidan ya duba ta. Tana shiga bayi ta fad'a ko lura da Hidaya da ke kwance a gado ba tayi ba, tsabar wanka ne kawai a gabanta. Hidaya kuwa gaba daya ta zurfafa cikin tunani, hotunan RJ ne take ta kalla, wanda ta saka ya turo mata su ta email, kallonshi take zuciyarta tana kuma ruruwa da zazzafar k'aunarsa wacce ta riga ta gama mata illa tun k'uruciya, tasan Mommy baza ta tab'a bari wata alak'a ta shiga tsakanin Nusrat da RJ inba, inma ta shiga akwai hanyar da zata bi ta sanya sabon almakashinta ta datseta, saboda itace take gaya mata RJ nata ne akwai alk'awarin aure tsakaninsu, tana gama makaranta za'ayi bikinsu, to amman Daddy fa? Tabbas Daddy idan yasan RJ in yana son Nusrat zai iya goya mishi baya ya aureta hakan yana nufi zasu had'a kishi da Nusrat kenan? Kai ina bazai yihu ba bama zai tab'a yuyuwa ba kawai dai za ta san duk yadda za tayi Nusrat in ta saurari Ishaq yadda maganarsu za tayi k'arfi tunkan dawowar RJ. "Hidaya kanne har yanzu? Ki tashi ki watsa ruwa kiyi sallah sai kici abinci kisha magani" Maganar Nusrat da ta fito daga wanka jikinta yana ta d'igar ruwa ta katseta daga tunanin da ta zurfafa a ciki, d'aga kai tayi ta kalli Nusrat in zuciyarta tana mata wani irin ciwo kafin ta amsawa Nusrat in da ka alamun taji me tace ba tare da ta bata amsar tambayar da tayi mata ba, itama,ba ta damu da hakan ba saboda ta san a hali na ciwo take sai kawai ta hau kimtsa jikinta. Ice cream in da suka siyo kawai tasha ta hayewarta gado, don yau ba ta jin cin abinci, wayar Hidaya da ta ajiye ta fita ta d'auka da yake ta san key in ta bud'e ta hau buga gem, can kuma sai ta lalubo number Auncl Iliya da ta saka tayi saving tun a washe garin zuwanta ta kirashi ya had'ata da Yusra, ta danna mishi kira, ringing d'aya zuwa biyu taji muryar Yusra tana fad'in. "Yayarmu" "Yusrata ya kuke, ya su Auncle Iliya da Aunty Hafsan?" "Lafiya lau Yayarmu, Aunty Hafsa ma ta haifi mace shekaranjiya." "Masha Allah, Allah ya raya, basu nayi musu barka." "Amin, tom bara na kai musu." Auncle Iliya ta fara bawa suka gaisa tayi masa barka kana ta bawa Aunty Hafsa itama suka gaisa tayi mata barka daga bisani Yusran ta karb'a suka cigaba da hirarsu, anan take gaya mata Auncle Iliya ta sanyata a makaranta private me kyau, kuma yace bayan suna zai siya mata waya k'arama da zasu dinga yin waya da Nusrat in, Farin ciki sosai Nusrat in ta shiga, ta dinga kwararawa Auncle Iliya Addua, sai taji zuciyarta ta nutsu guri d'aya da Yusran ta samu muhalli me kyau, a yadda Yusran take gaya mata daga Auncle Iliyan har Aunty Hafsa mugun ji suke da ita. Sun dad'e sosai suna hira cike da so da k'aunar junansu, syna jin kamar sunyi shekaru masu yawa rabonsu da juna, har Hidaya ta shigo suna wayarsu ta jinjina kai a ranta tana jinjina soyayya da shak'uwar da ke tsakanin Nusrat da Yusra, wanda su sam babu irin wannan shak'uwar tsakaninta da 'yan uwanta, amman kuma tana mamakin duk shak'uwar Nusrat da Shukhura a baya amman yanzu duk basa k'aunar ai musu zancen juna ta rasa dalili, duk kuma tayi musu wannan tambayar babu wanda ya bata amsa, haka rannan da suka had'u da Shukhura a Buk (Itama can take zuwa tana karantar lunguistic, medicine yaso nema mata Mustaphan amman bata samu ba.)tace mata Nusrat ta dawo gidansu da zama amman sai ta basar da zancen nata ta nuna kamar ba taji me tace ba, itama Nusrat in babu yadda ba tayi da ita akan tazo suje gidan Shukhuran tana Kuntau forestry amman fir tak'i, da ta d'auko zancen Shukhuran zata had'e mata fuska, kuma abin yana mugun damunta don tasha kamata da hotunansu su uku ko su hudu har Mama tana kuka tana meyasa Shukhura ta zabi yin KATANGA a tsakaninsu, duk ranar da tayi irin kukan nan kwana take tana sallah tana nemawa iyayanta rahama da kuma dawowar Shukhura cikin rayuwarsu. Suna gama wayar ta kashe ta mik'awa Hidaya dake zaune ta k'ureta da ido ta zurfafa a tunani, muryar Nusrat ince ta dawo da ita daga tunanin. "Gashinan, naji alamun an kiraki ki duba kiga wa ya kira." Karb'a tayi had'e da yin murmushi tace. " Soyayyar da Shak'uwar dake tsakaninku da Yusra tana birgeni ina jin inama nima da Hibba haka muke." Murmushi Nusrat in tayi had'e da fad'in. "Idan hakan yana birgeki lokaci bai k'ure miki ba, kafin barinki gidannan ki jaho Hibba jikinki ki nuna mata soyayya, to tabbas zata sake da ke za kuma tafi girmamaki da nuna miki soyayya." "Zan gwada" Ta fad'a a tak'aice had'e da mayar da hankalinta kan wayar don ganin waye ya mata miss call, Ishaq ta gani, tana k'okarin bin kiran ya kuma kira, picking tayi had'e da kwanciya akan gadon tayi rigin gine, yaya sukaje gida shine abinda ya tambayeta ya kuma ce mata kada ta manta ta turo masa Addres in gidan nasu tace masa insha Allah baza ta manta ba, suna gama wayar ta tura masa tana k'udirewa a ranta ko ta yaya ne sai ta cusa Nusrat din cikin rayuwarsa yadda zata bar mata Rj inta ita kad'ai..... Ina fama da rashin chargi shiyasa zaku dinga jina shiru. [4/26, 8:43 PM] Rabi: BEBE'ARTH KTG 25 Washe gari da Ishaq yazo masaukin bak'i Hidaya ta sanya aka kai shi, kana ta tura Hanne me aikinsu ta kai mishi juice da ruwa da d'an abin motsa baki daga bisani ta nufi gurin nasa ta bar Nusrat tana kintsawa bayan ta lallab'ata da dad'in baki akan taje ta saurareshi taji da me yazo, in yaso sai ta sanar da shi abinda ke ranta. Gaisawa sukayi cikin mutumci, kana ta sanar mishi Nusrat in tana shiryawa ne kafin ta zayyana mishi cewa ko da Nusrat in ta sanar masa akwai wanda taiwa kanta alk'awari to ba haka zancen yake ba, kawai dai tana tsoron maza ne saboda wani da ya yaudareta ana gab da bikinsu yace ya fasa, to amman ya bita a hakan, in yaso sai yace yana son su k'ulla abota, duk yadda dai zaiyi yayi ta anshi abotarsa ita kuma za ta dinga taimaka masa a hankula sai dai Nusrar in ta tsinci kanta cikin soyayyarshi, yayi na'am sosai da shawarar da ta bashi ya dinga zuba mata godiya yana k'ara ganin girma da kimarta. Itace da kanta taje ta taho da Nusrat in, daga bakin k'ofa ta tsaya tayi mata nuni da ta shiga ita kuma ta juya. Ta d'an jima sosai a bakin k'ofar kamar ta shiga kamar ba ta shiga ba, ta b'angaran Ishaq kuwa yaji tsaiwar mutum a bakin k'ofa da sabon k'amshin turaran da ya ziyarci hancinsa amman shiru yaji ba'a shigo ba, a hankali ya mik'e ya nufi bakin k'ofar, yana d'aga labulen itama ta d'aga kenan za ta shigo idanuwansu ya sark'e guri d'aya, d'an ja baya tayi a ranta tana yaba tsarin kyahunsa duk da bai kai Yaa Rj ba da wannan me kyahun da sukai karo har sau biyu a asibiti ba, mtsss taja tsaki a ranta ko meye na tuno shi kuma? Ja da baya yayi har lokacin idonsa bai bar kanta ba, yana jin yadda k'auna da soyayyarta ke karya kuzarinsa. "Bismillah zo ki shige." Ya fad'a yana me nuna mata hanyar da hannunsa, babu musu ta shige a sanyaye don idanuwansa sun fara kashe k'arfinta da ta fito da shi, bayan sun zauna gaba d'aya k'asa tayi da kanta tana mai gaisheshi cikin muryarta da ta k'ara yin sanyi wacce shi kuma ta k'ara sanyashi mutuwa sosai cikin k'aunarta, bayan sun gaisa babu kwane kwane ya zayyana mata abinda ke tafe da shi wanda itama ba tayi nauyin bakin sanar da shi akwai alkawarin wani a kanta ba inda shi kuma ya nuna mata buk'atarsa ta yin abotaka tunda ba ta amshi soyayyarsa ba, ita kwa tace sam babu abotaka tsakanin mace da namiji baza ta amsa ba, da k'yar dai ya shawo kanta akan in ya kira waya zata amsa ko ba ko yaushe ba, kuma in ya bukaci ganinta za ta amince ko da a wata sau d'aya ne ba ta amince masa ba sai da sukai alk'awarin bazai dinga kashe mata kud'i ba kafin daga bisani sukai sallama ya bata rafar 'yan dubu akan ta baiwa Hidaya, taso k'in amasa ta kuma nuna mishi zai fara karya alkawarinsu tun yanzu yace ai ba ita ya bawa ba Hidaya ya bawa. A haka rayuwa take juyawa tana tafiya, shekara ta zama tamkar wata, wata tamkar sati, sati tamkar kwana aya, kwana aya, kwana aya tamkar huni, anyi azumin watan ramadana cikin hukuncin Ubangiji, wanda suka dinga iban garar girkuna kala kala gurin Nusrat, don har searching in girkuna ta dunga yowa a wayar Hidaya,don ita kanta girkinma yana sanyata nishad'i kuma tasan kanta take taimaka don ta tabbata duk mijin da ya aureta to tabbas sai yayi alfahari da ita indai a b'angaran girki ne. Sam ba tayi wasa gurin ibada ba, ta mayar da hankali sosai tana rok'awa iyayanta rahama gurin Ubangiji, su kuma da kyakkyawar rayuwa a garesu tare da miji na gari, da kuma dawo da KATANGAR kaunar dake tsakaninsu da Shukhura. Har yanzu bata da waya babba, Daddy ne yaso siya mata amman Momy tace masa Nusrat in ba ta da ra'ayin rik'e babar waya gara ya siya mata k'arama, don ta sanshi mak'udan kudi zai saka ya siya mata wayar musamman yadda yake kwasar girkunanta masu dad'i, to shine ya siya mata waya 'yar k'arama me kyau me kuma tsada, dama tana da sim inta a ajiye ta d'auko ta d'orashi akai. Kud'in kayan sallah ma da ya tashi bayarwa kai d'aya duk ya bayar har Nusrat don sosai yake jinta a ransa kamar 'yar da ya haifa, amman Momy sai da ta zaftare rabi a na Nusrat in, amman duk da haka Nusrat in ba iya kanta tayiwa siyayyar sallar ba har da Yusra, ta kuma siyawa yarinyar da Aunty Hafsa ta haifa me suna Nuru kaya set biyar masu matuk'ar kyau da tsada duk a cikin kud'in nata amman Hidaya ce ta k'ara mata kud'in wanda itama Ishaq ne ya bata yace ta san yadda za tayi ta bawa Nusrat in ba tare da ta san shine ya bata ba. Uku ga sallah suka d'unguma sukai zariya, farin ciki duk ya cika zuciyar Nusrat burinta kawai ta isa mahaifarta ta ganta gata ga Yusranta, cikin Umma da Iya babu wanda yake ta ita, ko kuma ya nuna murnar canjawarta, don ba k'arya ta goge ta k'ara kyau musamman da take amfani da mayuka da aabulu da shower gel in da Hidaya ta siyo mata, sosai fatarta ta kuma gogewa kyahunta ya kuma baytana a fili, to duk bak'inci suka nuna mata a fili da habaicin da suka saba suna fad'in duk kwad'ayinta dai baza ta samu miji tamkar ya na Shukhura ba, babu wanda ta tankawa kamar ko yaushe ta janye jikinta ta nufi d'akinsu ta bud'e ta shiga da kayanta da na su Yusra da ta siyo musu. D'akin ta gyara komai yayi nead, kana ta nemi guri ta zauna, tana jin b'acin ran da su Iya suka sanyata yana damunta duk kwa k'ok'arinta na ganin ta kawar da shi ta yakice shi daga ranta, kallon d'akin nasu take sosai tana tuna rayuwarsu a ciki kamar yanzu komai yake faruwa cikin kwanyarta, rayuwa kenan, number Yusra ta lalibo ta danna mata kira saboda in ba haka ba kuka za tayi wanda kuma kukan bazai shafa mata lafiya ba. Wani wawan ihu Yusra ta saki yayin da Nusrat ta sanar mata tana cikin garin zariya. "Gani nan gani nan Yayarmu" Shine abinda take fad'i cikin zallar d'auki da farin ciki, katseta Nusrat in tayi akan ta bari gobe za tazo, k'in yadda tayi da k'yar ta lallasheta kana ta hak'ura, suna gama wayar, wayar Ishaq ta shigo mata don yaji ya suka isa zariyar. Washe gari tun da safe ta shirya ta yiwa Momy sallama akan ta tafi unguwar fulani, acan Uncle Iliyan yake a zaune, Hidaya taso yi mata rakiya amman ciwon kai take fama da shi don haka kawai tace ta gaishesu, yayin da suka tafi da Hibba da tace zata bita don itama tana son ganin Yusran. Tunda Nusrat ta sanar da Yusran suna hanya Yusra ta kasa tsaye ta kasa zaune, tana jin sallamarsu da gudu taje ta d'afe Nusrat in suka ruk'un kume juna cikin murna da farin ciki, yayin da Hibba ta tsaya tana ganin ikon Allah tana jin a ranta inama suma irin hakanne ke wakana tsakaninsu da Hidaya, duk laifin Momynsu ne da ta gina musu irin Katangar da Mamansu Yusran ta gina musu da yanzu hakan bazai bata sha'awa ba. A yau dai farin cikin Yusra da Nusrat bazai rubutu ba masu karatu ku hasasho kawai, musamman da taga irin siyayyar da Yayar tasun ta jibgo mata, duk da yanzu Alhmdlillh duk wani abin buk'ata Auncle Iliya yana iya bakin k'ok'arinsa ba k'aramar murna tayi ba ta dinga jero mata addua tare da iyayansu da suka rasa. Aunty Hafsa ma tayi murna ga kuma kayan da ta bayar a sakawa Nuru, godiya ta dungai mata, tana k'ara ganin girma da kimar Nusrat in tare da jinjinawa mahaifiyarsu da yi mata adduar dacewa. Ko da suka tashi tafiya Yusra had'o kayanta tayi akan za ta bisu, in yaso in suka tafi ta dawo, amman Nusrat ta hanata, duk da k'asan ranta tana son kasancewa da k'anwar tata, kuka sosai Yusran ta samu guri tana yi kamar k'aramar yarinya,ganin haka yasa Aunty Hafsa ta d'au waya ta kira Auncle Iliya ta sanar masa abinda ke faruwa kawai yace suje din in sun tafi ta dawo. Tsalle da murna Yusran ta hau yi yayin da Aunty Hafsan ta gaya musu abinda Auncle Iliyan yace. Satinsu d'aya da zuwa zariya Shukhura ma suka zo, tazo gidan da sha tara ta arzik'inta wanda Umma ta dinga yadarwa da su Nusrat in magana, Yusra taso tankawa Nusrat in ta hanata, huni ranar Shukhura tayi a gidan amman ba ta neme su ba suma basu nuna sun san da zuwanta ba, Nimha kuwa da tazo har d'akin da suke ta shigo suka gaisa, don haka suma suka saka rana suka je gidanta har da su Hidaya suka huni sur a can, don su Nimha anyi kud'i ana ta fantamawa. Satinsu biyu cur a zariya suka tarkata nasu ya nasu suka tafi, Yusra da Nusrat suna ta kewar juna, don sati biyunnan da sukayi tare ya tayar musu da tsimin abubuwa masu yawa, har ba taso tafiyarsu ba tayi tunanin wata guda zasui, duk da yanzunma Momy tace Daddy ne yace su dawo saboda Rj jibi zai dawo kar ya dawo gidan ba kowa, duk da tasan Daddynma a matse yake da su dawo don ya gaji da kame kamen abinda yake ci·.... Juma'a asabar lahadi zaku jini shiru· [4/26, 8:44 PM] Rabi: BEBE'ARTH KTG 26 Ana ya gobe Rj zai dawo Hidaya ta tsame jikinta ta tafi saloon akai mata gyaran jiki da na kai, Nusrat kallonta kawai take yadda take ta rawar kan dawowar Rj in, hatta kayan da zata saka sababbi ne ta siyo su, zuciyarta ta fara zargin anya Hidaya da Rj in ba soyayya suke ba ya ninketa a bai bai yasa ta mishi alk'awari amman ko ma dai meye za ta zuba ido taga dawowarsa da wani taku zaiyi, idan kwa ya tabbata Hidaya son RJ take to tabbas zata haramtawa kanta shi tun kafin a haramta mata zuciyarta ta samu matsala. Biyar da rabi na yamma Hidaya da Daddy suka tafi filin jirgi taro Rj saboda yace shida dai dai jirginsu zai sauka, shidan kwa a filin jirgin tayi musu hakan yayi dai dai da isowar jirgin nasu, idanuwa waje Hidaya ta zuba tana jiran saukowar annurin zuciyarta. Murmushi kwance akan kamilalliyar fuskarsa ya fara saukowa daga jirgin yana wurga idanuwansa ra inda zai hango Daddy, idanuwansa akan Hidaya suka sauka wanda itama nata idanuwan akansa suke zuciyarta tana wani irin bugawa had'e da yamutsawa da zallar soyayyar yayan nata, murmushi ya sakar mata wanda ya kuma matar da ita a zallar k'aunarsa kafin ta sakar masa nata murmushin shi kuma a lokacin ya d'auke idonsa daga kanta ya mayar kan Daddy da ke gefenta suka sakarwa juna murmushi kafin ya nufo gurin da suke a tsaye. Rungume juna suka yi da Daddy, yana jin soyayyar d'an d'an uwan nasa na kuma huda ko wata k'ofa ta zuciyarsa, yana jinsa sosai cikin ransa kamar shine ya haifesa, yayin da shima Rj in soyayyar Daddyn nasa ke kuma ninkaya cikin zuciyarsa, shi maraya ne amman baisan wani abu maraici ba, duk wata k'ofa da zata sakashi tuna shi maraya ne Daddy ya toshe masa ita, Daddyn yakewa kallon mahaifinsa tunda da shi ya tashi ya bud'i ido mahaifinsa ya rasu ba tare da ya mallaki hankalinsa ba sai Allah ya bashi wani mahaifin wanda suka shak'u da juna yake kuma share masa hawayensa a duk sanda sukai kokarin zuba. Kallonsa Hidaya take kamar ta lashe shi, ya k'ara kyau ya k'ara girma fatarsa ta goge ya zama ingarmar namiji, wani sonsa da k'aunarsa take ji yana kuma shiga ruhi da zuciyarta, ashe hotunan da ya turo mata b'oye wani kaso daga kyahunsa sukayi. "Hidaya na canja miki ne?" Rj ya jefo mata wannan tambayar ganin irin kallon da take masa, wata kunya ce ta kamata ta rufe fuskarta da hannuwanta tana dariya kafin tace."Allah Yaa Rj ka canja sosai, kamar ba kai ba." "Ke ba kiga canjawar da kikayi ba kenan sai tawa?" Wani dad'i ne ya ziyarci ruhinta cike da jin dad'i tace. "Dan Allah Yaa Rj na canja?" "Kin canja mana, tunda ba haka na tafi na barki ba." "To wata iriyar canjawa nayi." Tana so taji yace ta k'ara kyau ne, kamar yadda ta gani a tare da shi, muryar Daddy ce ta katsesu da cewa. "Ku muje gida mana, in munje kwayi hirar." A ransa yana adduar Allah ya cika masa burinsa ya had'a zuciyoyin Hidaya da Rj in guri guda. Sai da ya fara shiga suka gaisa da Mommy, Abbas da Hibba sukai masa barka da dawowa kana ya fito ya nufi phart insa da ke gefen gidan zuciyarsa cike da murad'in ganin Nusrat, yana mamakin rashin ganinta da baiyi ba kuma ba ya son tambayar Hidaya don ya fuskanci ba ta so, tunda babu yadda baiyi da ita akan ta had'ashi da Nusrat in a waya tak'i ba, kullum da k'aryar da zata shafto masa, haka da yace ta d'au hotonta ta turo masa ta shiriritar da zancen, ya rasa inda Hidayan ta saka gaba, shi dai a iya saninsa bai taba nuna mata wata alama ta yana sonta ba don shi zuciyarsa Nusrat kawai take so da ita kad'ai yake jin zai iya rayuwa, kwana yake yana mik'awa Allah kukansa akan yabar masa Nusrat insa ba tare da wani ya aureta ba har ya dawo, sai gashi Allah ya amshi adduarsa, Nusrat ta rik'e alkawari da yardar ubangiji. Wanka yayi da ruwa mai zafi yadda zai huce gajiya, ya d'auro alwala ya fita masallaci bayan ya shirya cikin black in jus da red in t shirt a gaggauce kar ya rasa jam'i, a masallacin ya zauna har sai da yayi sallar isha kana suka shigo cikin gidan tare da Daddy suna tab'a hira a tsakaninsu duk akan aikinsa da cigaban da ya samu, shekararsa biyu da gama karatunsa suka rik'esa a can yayi musu aiki saboda kaifin basira da k'wak'walwar da Allah ya bashi, yanzu ma sun so cigaba da rik'e shin yak'i yarda gaba d'aya hankalinsa yayo gida, shekara uku sukayi da Nusrat sai gashi ya d'ebi shekaru har biyar, inda Allah ya taimakeshi ma ta rik'e masa alk'awarinsa wanda bai tsanmata ba ganin ya sab'a k'aida. A dining sukayi masauki, Hidayace yau tayi serving in kowa da k'ayataccen girkin da Nusrat in tayi saboda RJ inta. "Yau ina Nusrat in?" Daddy ya fad'a yana kallon Hidaya, wanda ya nuna ita yakewa tambayar, d'an sosa kanta tayi kafin tace. "Cewa tayi kanta na ciwo ba za ta iya fitowa ba." Mayar da kallonsa yayi kan Hibba kafin yace. "Maza jeki ki kirahomin ita." Rj ji yayi kamar Daddy ya tsunduma shi a aljanna da ya tura a kiraho hasken idaniyarsa. Ina fama da rashin chargi shiyasa kuke jina shiru, ni kaina na k'agu naga munyi nisa cikin labarin amman ko tsakiya ba muzo ba, idan komai ya daidaita zakuna jina sosai da sosai na gode. [4/26, 8:44 PM] Rabi: BEBE'ARTH KTG27 Waya suka gama da Yusra, sai ta fara yin game a k'aramar wayarta, saboda ji tayi sam ba ta buk'atar fita cin abincin ba ta san ya gamuwarsu da Rj zata kaya ba, jin za'a murd'a handle in k'ofar yasata d'aga kanta don ganin me shigowar, Hibba ce ta shigo da sallama a bakinta, Nusrat ta amsa mata tana mayar da kanta kan wayarta. "Aunty Hidaya ce tacewa Daddy wai kanki na ciwo, shine yace nazo na kiraki." Hmmmm Hidaya me take nufi da ni ne, don kawai ba ta son na fita mu had'u da Rj har sai tayi mini k'aryar ciwo? Shine tambayar da Nusrat kewa kanta, kafin tacewa Hibban. "Kicewa Daddy na samu bacci kawai." "Toh" Ta amsa mata da shi ta fita. "Ta samu bacci." Shine abinda ta cewa Daddy, kai kawai ya d'aga mata saboda ya fara cin abinci, yayin da Rj bai yadda da zancen Hibban ba, to tunda tak'i fitowa shi zaije har d'akin ya same ta, bayan Daddy ya kammala cin abincin ya kalli Hidaya da ke ta cin abincin cikin yanga saboda do take kowa ya fashe a barta daga ita sai Rj intadon shima ta fuskanci cin yangar yakewa abincin,yace. "In kin gama ki iba mata abincin, ga awararta nan, ki tabbata kin tasheta taci tasha magani." Da "Toh" Ta amsawa Daddyn da ya tashi ya bar dining in Mommy ta mara masa baya saboda ta gama itama, Hibba da Abbas suka tashi kowa ya nufi d'akinsa ya zamto sai su biyu kad'ai akan dininin in, a hankali ya mik'e don dama ya k'oshi da abincin jira yake a bashi guri, plate ya d'auka ya zuba abinci d'an dai dai kana ya d'auki awarar da Daddy yace ta Nusrat ce ya haye sama, baki sake Hidaya ta saki tana kallonsa har ya gama haye matattakalar. Gajiya tayi da game in don haka ta kashe ta gyara kwanciyarta sosai akan gadon ta ja duvet ta rufe rabin jikinta, a hankula ta lumshe idanuwanta ta luntsuma cikin kogin tunanin nemo mafitar zuciyarta akan soyayyar Rj don yadda taga take taken Hidaya yafi kawai ta sanyawa kanta ruwan sanyi ta hak'ura da shi, tun da dama ba wai cewa yayi yana sonta ba itace take haukanta. knocking yayi murya can k'asa tace. "Shigo." Tana tunanin Mommy ce don itace me yi musu knocking kafin ta shigo, a hankula ya turo k'ofar ya shigo idanuwansa gaba d'aya suka sauka cikin nata, a lokaci d'aya bugun zuciyoyinsu suka sauya, kallon cikin idonta yake sosai wanda ta kasa jurewa hakan ta kautar da kanta gefe, wani d'an k'aramin center table ya janyo ya d'ora plate in da ledar awarar, sai da yayi gyaran murya kafin yace. "Ni gani nazo tunda guduna ake, saboda ni anki saukowa cin abinci to gashinan abincin ya biyo ki sai ki d'auka ki ci." Bagarar da zancen nashi tayi da cewa. "Ina wuni, an dawo lafiya.?" "Tambayeni kiji." "To ai tambayar taka nayi." Baice mata komai ba ya hau dube dube d'aga can duba can kallonshi tayi da mamaki had'e da fad'in. "Wai me kake nema?" "Murmushinki nake nema, so nake na lalibo shi a duk inda kika b'oyeshi saboda nayi kewarsa mara misali." Wani bazataccen murmushi ne ya sub'uce mata had'e da wata siririyar dariya, dariyar shima yake ya tsaya yana mata wani narkakken kallo kafin cikin wata murya mai shauk'i ya kira sunanta. "Nusrat." A hankali ta d'ago kanta idanuwansu suka gauraya guri guda, wani maganad'iso ne yake janshi daga cikin idanuwanta ji yake idan bai furta abinda ke k'irjinsa shekaru masu yawa ba yana k'ara yin nauyin da ke k'ok'arin yi masa illa gaba d'aya ba kamar numfashinsa zai rabu da gangar jikinsa ne, cikin wata shauk'ak'k'iyar murya tace. "Ilove you Nusrat, ban san da wani baki zan gode miki ba, kinyi namijin k'ok'arin da ba ko wacce mace ce zata yishi ba, kin toshe kunnuwanki daga jin gori da habaicin rashin aure saboda cika alk'awarin da kika d'aukar mini duk da ni na sab'a k'aidar k'ara shekaru biyu kan ukun da na ibar miki wanda nima ba a son raina hakan ya faru ba, ban tab'a tunanin zan dawo na tarar kina jiranaba sai gashi kin bani mamaki, tabbas na jinjina miki jinjina ta ban girma sarauniyata, ina so a bani damar da zan shayar da ke ruwan soyayyata mai gard'i wacce na dad'e ina tanadinta da b'oyeta duk saboda ke Nusrat." Zuciyarta wani irin bugawa take da sauri, tana jin yadda take bud'ewa da karb'ar sak'on soyayyar Rj in me girma, ashe da ba jin sonsa take ba,yanzu ne take jin aininhin soyayyarsa cikin zuciyarta wanda ba ta shiryawa hakan ba saboda hango tari matsalar da ke gabansu amman da dukkan alamu zuciyarta ta shiryawa hakan ba tare da tabi shawararta ba, wani irin yanayi take ji a cikinta mara misaltuwa." "Kinyi shiru Nusrat, kice wani abu mana pls." Ya fad'a da karyayyar muryarsa yana kallonta. Momy ce ta sauko daga benen Daddy ta tarar da Hidaya ita kad'ai a zaune akan dininng tayi zurfi cikin tunani, ranta gaba d'aya a dagule, d'an zungurunta Momy tayi had'e da fad'in. "Ke kuma lafiya kowa ya tashi ya bar ki a zaune, me kike zaman jira ina Rj in?" D'an sosa kanta tayi tana b'oye yanayin da zuciyarta ke ciki tace. " Shine yace na jirashi yaje ya dawo." "Ok" Mommyn tace tana hayewa samansu, ajiyar zuciya Hidaya ta sauke tana jin yadda zuciyar tata tayi mata nauyi, number Ishaq ta lalibo ta danna masa kira ta sanya ta free kana ta haye saman ta murd'a handle in k'ofar a dai dai sanda Rj in ya kuma fad'in. "Pls Nusrat, say something mana" Yakai k'arshen maganar yana dak'una fuska, kafin gaba d'aya su zubawa k'ofar ido don ganin me shigowar, zuciyar Nusrat na bugawa da tsoron ko Momy ce, ganin Hidaya ce yasata sakin b'oyayyar ajiyar zuciya, mik'o mata wayar Hidaya tayi had'e da fad'in. "Ishaq ke magana." Don a lokacin muryarsa ta bayyana tarwai yana. "Hello." K'irjinta yana wani irin bugawa ta karb'i wayar cikin sanyin muryarta tace. "Salamu Alaikum" Jin muryar Nusrat ya sanya Ishaq cikin wani matsanancin dad'i, yau shi Nusrat ta kira akan k'ashin kanta, tabbas dole yau yayiwa Allah godiya da yasa ya fara samun matsayi gurin Nusrat in,muryarsa cike da zallar farin ciki yace. "Wa'alaiki salamu da My Nuss, da fatan dai kina cikin k'oshin lafiya?" Wayar ta ciro daga kunnenta ta kalla kafin ta d'aga kai ta kalli Rj da ya mik'e tsaye cikin matsanancin b'acin ran da ya kasa b'oyuwa akan kamilalliyar fuskarsa, zuciyarsa wani irin tuk'uk'i take masa mai zafi ya bud'e k'ofar ya fice, Hidaya ta bi bayansa d'auke da b'oyayyen murmushi.... [4/26, 8:45 PM] Rabi: BEBE'ARTH KTG28 Da sassarfa ta had'a ta taddashi a farfajiyar tsakar gidan yana dosar inda sashensa yake saboda tsabar saurin da yake zubawa. "Ai Yaa Rj Nusrat da Ishaq suna matuk'ar son junansu, kuma wallahi mutumin kirki ne sosai, yanzu haka ma maganar kawo kud..." Ba ta k'arasa ba sakamakon wata muguwar tsawa da ya daka mata wacce ita tayi sanadiyar had'iye sauran maganar tata, da hannu ya nuna mata hanya yana jifanta da wani mugun kallo na tambayarki nayi, ko ni sa'anki ne, ina wasa da ke? Sim sim ta shige idonta yana cikowa da k'walla yayin da shi kuma yaja tsuka yayi gaba zuciyarsa tayi bak'ik'k'irin, rigin gine ya kwanta a kan gado ya zubawa pop ido kamar yana karantar yadda aka zana shi yayi masifar kyau amman ba haka zancen yake ba, tunaninsa gaba d'aya yana kan Nusrat, bai jin zai iya jure rad'ad'in rasata ko kad'an, bai san so ko k'auna ba sai a kanta,a kanta zuciyarsa ta fara bud'ewa kuma yana jin akanta za ta rufe har abada, a komai nasa ita yake gani cikin idanuwansa kamanninta kuwa sun dad'e da mannewa cikin idanuwansa, yana mugun sonta, idan yace so yana nufin so na hak'ik'a wanda babu d'igon algus a ciki. Bazan iya jure rashinki ba NUSRAT ki taimakeni ki gaya mini ba ki bud'ewa kowa zuciyarki ba sai ni don Allah na rok'eki ba don ni ba kar ki karya alk'awarin da nake murnar kin rik 'e mini shi. Abinda yake sak'awa daga can k'asan zuciyarsa kenan yayin da wani b'ari na zuciyarsa yake jin kamar gaske ne maganar da Hidaya ta gaya mishi, tun da lokacin da yake saurarar jin ta bakinta shiru tayi masa alamu kenan na ta riga ta bud'ewa wani zuciyarta, kai ina ba haka bane tana dai da wani dalili nata. Bayan fitarsa zubawa wayar ido tayi da Ishaq yake ta faman hello hello da ya gaji ya kashe wayar, rintse idanuwanta tayi tana jin yadda jijiyoyin kanta suke mik'ewa. Innalillahi wa inna ilaihir rajiun shine abinda take ambata cikin ranta ko za ta ji zafi da rad'ad'in da zuciyarta take zai ragu, sai yanzu ta fuskanci dalilin da yasa Hidayan ta mik'o mata wayar saboda ta gane itace ta kira Ishaq d'in ba shi ya kirata ba, tayi hakanne don ta b'ata tsakaninta da Rj yayi mata kallon me karya alk'awari tun da ta gaya mata shine wanda ta yiwa alkawari, sam ba ta d'au Ishaq a matsayin saurayi ba sai dai tana bashi girma saboda yadda yake hak'uri da ita da bata kulawa duk da shi yaga zai iya hakan, to hakanne yasata karb'ar wayar tunda ba ta san me zaice mata ba may be kuma ya kira wayarta yaji ta a kashe don da ta gama game in kasheta tayi gaba d'aya, ba tayi tunanin wayar a speaker take ba da kuma Rj in bai san tsakaninta da Ishaq ba, amman za tayi k'ok'arin fahimtar da shi kada yayi mata kallon me karya alk'awari. Da wannan abin da Hidaya take gara tazo ta tareta suyi me yuyuwa yafi, amman tunda haka ta zab'a to itama za ta zuba mata idanuwa taga inda wasan nata zai tsaya, ita dai baza taki amsar soyayyar Rj ba saboda dama ita take jira don ta tura shirmen mafarkinta gefe, sai dai tana tsoron inda makomarsu za ta tsaya saboda ga Momy ga Hidaya a gefe, don ta tabbata Momy ba za ta bar 'yarta ta zab'eta ba amman ko ma dai meye Allah ba ya bacci, idan har Rj mijinta ne zai kawo musu hanya mafi sauk'i. Washe gari ko break bai tsaya yayi ba ya d'auki hanyar kaduna dama al raedy Daddy da Mommy sun san da tafiyar tasa, Hajiya, (Haka suke kiran mahaifiyar tasu da k'annensa mata guda biyu da ta haifa a kadunan, suma dukkaninsu sunyi aure ko wacce tana da yara bibbiyu) tayi matuk'ar farin cikin ganin d'an nata, hakama k'annen nasa Safiya da Hafsa ko wacce tazo don ganin d'an uwan nasu don sun san halinsa na son girma da manyance sai yace bazai je musu ba duk da zolayar da suke masa yanzu na sun girmeshi dole ya basu girman saboda sun rigashi dire 'ya'ya. Bai baro kaduna ba sai cike da tarin k'aunar mahifiyarsa da 'yan uwansa sai dai zuciyarsa cike take da tashin hankalin abinda yaji daga bakin Hajiyarsu wanda ko da wai bai tab'a hasasho hakan ba, ta sanar mishi ne akan maganar Aurensa shi da Hidaya nan da shekara d'aya idan Hidayan ta kammala karatunta, duk da ita Hajiyan ta so yana dawowa yayi aure sai dai sunyi maganar da Daddy inda yake ce mata so yake Hidayan ta kammala karatunta shekara me zuwa ya had'asu aure don yaga alamun ma sun dai daita kansu, farin ciki sosai Hajiyan ta shiga don Daddy mutum ne ba abun yadarwa ba, had'a zuri'a da shi kuwa babban rabo ne, kasa rik'e farin cikin nata tayi shiyasa da Rj in yazo tayi masa zancen, ganin tarin farin cikin da mahaifiyar tasa take ciki ne yaga bazai iya katse mata shi ba kawai yabita akan hakane, amman fa zuciyarsa gaba d'aya a cunkushe take tunaninsa ya katse ya rasa wani irin tunani zaiyi. Yana doso hancin motarsa harabar gidan idonsa ya sauka akan Nusrat da Ishaq suna tsaye da alamu sallama suke zai tafi don a jikin motarsa suke a tsayen, hankalinsa ne ya kasa kwanciya da yai ta kiran wayar ba'a peking, Hidaya da ta shigo taga tarin miss call insa sai tayi masa tex akan yazo gobe tana son ganinsa a zuwan Nusrat ce ta tura masa shi kuwa Ishaq ganin wannan tex in sai ya kwantar masa da hankali ya kuma tsundumashi cikin farin ciki don ya fara ganin alamun nasara daga Nusrat in, kuma dama yana son zuwa ya ganta don ya kwana biyu bai zo ba gashi zaiyi tafiyar da bai san kwanaki nawa za ta ibeshi ba. Nusrat kuwa tana tsaka da had'a dinner ya kirata gashi ya k'araso, ta shiga d'inbin mamaki don ba suyi da shi zaizo d'in ba to amman sai taji ba za ta iya wulakanta shi ba tun da har ya riga yazo, Allah ya taimaketa ta kusa gamawa sai ta k'arasa a gaggauce ta bar Hibba da jerawa akan dinning, dama a shiryanta take cikin bak'ar doguwar riga da ta kuma fito da hasken fatarta, turare kawai ta kuma fesawa ta d'auki siririn jan mayafi ta yafa ta fita fuskarta na bada wani annurin kyahu. Sun d'an tab'a hira ba laifi aka fara kiran sallar magariba ya tashi zai tafi shine ta yo mishi rakiya bakin motarsa. Wani irin duhu Rj ya fara gani cikin idanuwansa yana jin wata sabuwar damuwar na kuma ninkaya cikin zuciyarsa, ko parking bai dai daita sosai ba ya fito yana rik'e kansa da ke mugun sara masa a hankali yake tafiya ya nufi sashensa, Nusrat kuwa hankalinta gaba d'aya yana kansa har Ishaq ya shiga motarsa ya ja ya tafi da sassarfa tabi bayansa tana kiran sunansa amman ko nuna alamun yaji bai yi ba da gudu ta had'a tasha gabansa tana d'an haki na gudun da tayi, d'ago da rinannun idanuwansa yayi ya aza a kan kyakkyawar fuskarta, kallon cikin ido sukewa juna, a hankula yaji zuciyarsa tana sanyi duk wata damuwa tana kwaranyewa saboda abinda yake karanta cikin idanuwanta, zare idonta tayi daga cikin nasa saboda yadda taji kuzarinta yana karkaryewa had'e da karsashinta, zoben da ya saka mata ta murza ta d'ago da hannun ta nuna masa had'e da fad'in. "Ka saka nayi maka alk'awari ba tare da ina da tabbacin sona kake ba, haka nayi k'ok'arin cika maka shi tare da jure dukkan wani k'unci, saboda rashin cika alk'awari alamace ta munafiki, amman sai gashi da rashin fahimta za ka saka mini, Ishaq ba saurayina bane, ya dai nuna yana sona ban amince masa ba na gaya mishi da alkawarin wani a kaina, sai ya buk'aci yin abota da ni naso k'in amincewa amman ya kafa mini naci na barshi a zuwan idan ka dawo mayi rabuwar mutumci da shi saboda ba ka san halin mutum ba. Akan ka zuciyata ta bud'e, kaine ka fara shiga cikinta ka samu babban masauki ina fatan kuma akanka za ta rufe idan ka bata damar hakan." Tana kawowa nan ta juya za ta tafi. "Nusrat" Ya kira sunanta, d'an dakatawa tayi ba tare da ta juyo ba. "Kiyi hak'uri don Allah." "Laifi indai naka ne ba ya zama a zuciyar Nusrat, musamman wannan da rashin fahimta ne kawai, har an tayar da sallah bara na k'arasa ciki." Wani kyakkyawan murmushi ya saki yana bin bayanta da kallo da ta wuce ba ta jirayi me zaice ba, ina sonki Nusrat yaji zuciyarsa ta ambaci hakan kafin ya shafa kansa ya nufi sashensa cike da karsashi da sabon kuzari, don duk sai yaji wata damuwa tasa ta yaye kawai zai tunkari Daddy da maganar yana son Nusrat tun kafin ya tunkareshi da maganar Hidaya don bazai iya kaucewa hakan ba saboda matsayi da kimar Daddyn a gurinsa, ita kuma Hajiya ya san ta yadda zai b'illo mata..... [4/26, 8:45 PM] Rabi: BEBE'ARTH KTG29 Wata sanyayyar soyayya ce ta fara gudana tsakanin Nusrat da Rj wacce sam Mommy ba ta ankara da ita ba saboda ba kasafai take sakkowa k'asa ba, tana da komai na buk'ata a cikin d'akinta, abinci kuwa Nusrat ce ke kai mata ta kuma sakko da kwanukan, sai yamma take sakkowa ta koma sashen daddy saboda tararsa shine sai a had'u ayi dinner tare, yanzu kuwa da Daddy ba ya nan dinner ma ba ta sakkowa a d'akinta take wuni sir abinta tana karatun novel idan 'yayan suna bukatarta sai suje gareta, duk da babu wata shak'uwa tsakaninsu saboda ba ta ginosu akan haka ba. Tafiya ce ta kama Daddy dalilin da yasa kenan Rj bai tare shi da maganar soyayyarsa da Nusrat ba ya bari ya dawo tukunna in yaso sai ya sameshi da maganar don ba ya fatan shi ya rigashi yi masa maganar Hidaya don bazai iya kaucewa hakan ba, sannan kuma a yadda yake jin soyayyar Nusrat bazai tab'a iya kwatanta rayuwa babu ita ba yana jin kawai sai dai ya had'asu su biyun ya aura idan hakan ta faru. Ko da wasa bai tab'a bari Nusrat in tasan da maganar aure tsakaninsa da Hidaya ba don yasan muddun ta san hakan tabbas za ta ja jiki da shi, haka ma Hidayan sam bai nuna mata yasan abinda take nufi da shi ba duk kwa na k'okarinta gurin nuna mishi irin tarin soyayyar da take masa sai ya dinga kakkauce mata yana nuna mata shi sam bai gane me take nufi ba Nusrat itace zab'in zuciyarsa. Tsakanin Hidaya da Nusrat kuwa babu abinda ya canja, don Hidaya tana k'okari gurin danne zafin Nusrat in da take ji saboda zumunci, amman dai ba ta fasa cusa Ishaq cikin rayuwar Nusrat in ba saboda ta bar mata Rj dinta don a yanzu tayi amannar muddun Nusrat na nan ba ta ishi Rj kallo ba indai a barin soyayya ne, don haka ta d'au alkawarin sai tayi silar da Nusrat za ta auri Ishaq ko da ba ta so ta hakanne itama za ta samu muradinta, shiyasa ta k'agu Daddy ya dawo domin ta fara shirinta. Nusrat kuwa gaba d'aya ta gama karantar Hidayan tsaf son Rj take, wanda shima Rj in ta lura yasan da hakan kawai yana kakkauce mata ne, Allah ya gani tana son Rj so ba na wasa ba shima kuma yana sonta wannan dalilin ne yasa ta biye mishi suke soyayyarsu amman fa can k'asan ranta tsoro ne fal cikinsa musamman sanda Rj in ya rarraba musu tsaraba ita har da tanfatsetsiyar waya ya bata wacce ya siyo mata ita ta musamman to da taje nunawa Momy sai ce mata tayi. ‘’ Ki dai tsaya matsayinki banda shishshigin shiga hurumin da ba naki ba domin ba dake ya kamata ba, idan kuma kinki ji duk abinda ya biyo baya babu ruwana." To wannan ne yake sawa wani zubin duk sai ta sare tana hango tafiyarsu da Rj in babu inda zata je wanda hakan itakam bazai shafa mata lafiya ba, duk da Rj in yakan kwantar mata da hankalin Daddy yana dawowa zai sameshi da maganar auransu don ba lokaci yake so a jaa, to idan tayi laakari da sauk'in kan Daddyn wanda tayi amannar bazai hanashi auranta ba sai taji hankalinta yana d'an kwanciya. Wata d'aya Daddy yayi ya dawo wanda yazo ya tadda familyn nasa cikin murna da d'aukin dawowarsa sai ya alakanta hakan akan bai tab'a yin kwanaki irin haka ba idan tafiya ta sameshi. A daren da Daddy ya dawo Hidaya ta d'au wayar Nusrat tayiwa Ishaq tex akan ta amince da shi gobe ya turo magabatansa gidansu sak'o inji Daddy, sai da ta tabbatar ya shiga kana ta goge ta saka number tasa a black list kana ta ajiye mata wayar cike da zallar farin ciki tana ganin tarkonta kamar ya gama danuwa. Ishaq da yaga message in Nusrat ya shiga matuk'ar farin ciki duk da kasan ransa yana mamakin anya kwa Nusrat ce tayi mishi wannan tex in don sun riga sunyi sallama ya daina kiranta ma don ta sanar mishi wanda za ta aura ya dawo kuma ba ya son muamalarsu don haka sai yayi mata fatan alkhairi yazo ya fara jinyar cire soyayyarta a ransa don yanzu yayi amannar ya rasata kenan har abada sai kuma gashi tex inta ya riskeshi a yau don gaka baiyi k'asa a guiwar danna mata kira ba amman sam tak'i shiga don haka sai ya juya akalar kirannasa ga number Hidaya. Gaisawa sukayi bayan nan ya buk'aci ta had'ashi da Nusrat tace masa tayi bacci da yake kanta na mata ciwo, nuna rashin jin dadin ciwon kan nata yayi kafin ya tambayeta game da tex in da Nusrat in ta turo masa, nan ta k'ara masa k'arfin guiwa had'e da tabbatar masa gaskiya Nusrat in ta fad'a don gobe ma an shirya tarb'arsu. Cikin zallar farin ciki Ishaq yajishi yana yawo don haka a wannan dare yaje ya samu mahaifinshi ya gaya mishi, sai dai mahaifin nashi yace zasuje amman tambaya kawai zasu yi sai anyi bincike kafin su kai kud'i. Hidaya suna gama waya da Ishaq tayi tsalle ta dire don ita kad'aice a dakin Nusrat ba ta shigo ba suna can tare da Rj, Hijabi ta saka ta nufi sashen Daddy, shi kadai ta tarar a kishingide yana cin tufa yana kallon tsofaffin fina finan indiya a cumpuiter insa. "Daddy Nusrat ce ta aiko ni." "To ina jinki." Yace mata yana gutsirar tufarsa. "Dama manema auranta ne suka ce zasu zo gobe, shine tace kunyarka take ji ni nazo na gaya maka." "Wannan yaron da yake zuwa gurinta?" "Eh shine Daddy" "To masha Allah, Allah ya nuna mana goben ya kawosu lafiya, amman me yasa momynku ba ta sameni da maganar ba? "Amin Daddy, ai itama ba ta sani ba yanzu in na fita daga nan zanje na shaida mata, kunyar Nusrat ce tayi yawa. "Ni na shaida hakan, Allah yayi muku albarka gaba d'aya, in kinje ki turon Momyn taku da alama yau ta manta da ni." " Amin, tom zan turota." Daga haka ta fice daga sashen cike da zallar farin ciki, a kwance ta tarar da Mommyn tasu tana karatun novel, wani littafi take karantawa K'addar rayuwarmu, ya d'auki hankalinta sosai ko d'auke idonta daga kan wayar ba ta son yi shiyasa ba tajewa Daddy ba don ta san bazai barta tab'a wayar ba musamman da yau ya dawo daga tafiya kuma tana son jin k'arshen littafin shiyasa ta bari in ta gama sai ta tafi gaba d'aya. Idonta akan wayar ta amsa sallamar Hidayan, gefen gadon ta samu ta zauna tana sauke idonta kan mahaifiyar tasu da babu ruwanta da lura da damuwoyinsu myddun in ba sune suka zo suka gaya mata ba. "Mommy magana nake so muyi." Ta fad'i hakan da sanyi a muryarta, haka kawai sai taji tana son bawa 'yar tata hankalinta don haka sai ta ajiye wayar tamik'e zaune tana sauke idonta akan Hidayan kafin Hidayan tace. "Momy kince akwai maganar aure tsakanina da Yaa Rj amman shi Nusrat yake so, yanzu haka ma soyayyarsu suke sha abunsu, ni kuma Mommy ina mugun sonshi soyayyar da tayi mini muguwar illar da ban jin zan iya warkewa don haka naji bazan iya barwa Nusrat Yaa Rj ba don na fita buk'atarshi shiyasa nayi amfani da Ishaq saurayinta don ya aureta na samu ta bar mini muradina don idan soyayyarsu taje kunnen Daddy zai aura mata shine ni kuma sai dai sonshi yayi ajalina." [4/26, 8:46 PM] Rabi: BEBE'ARTH KTG30 Shiru Mommy tayi zuciyarta na wani irin tafarfasa, tun da tazo ta nuna mata irin kayan da ya bata ta fara zargin wani abu tsakaninsu duba da shakuwarsu tun kafin tafiyarsa makaranta dalilin da yasa kenan tayi mata gargad'i gargad'in da ba taji ba kenan. "Me yasa tunda kika fahimci suna soyayyar ba kizo kin gaya mini ba?" Ta fad'i hakan tana sauke idonta akan Hidayan wacce gaba d'aya ta zama wata iri saboda rashin nutsuwa amman ta kasa ganin hakan wani irin b'acin rai taji yana taso mata zuciyarta tana zafi. "Ay nayi tunanin kin sani, sai daga baya na lura,ba ma kisan abinda ke faruwa ba ." Hidaya tace da ita haka. "Jeki ki kira mini ita." Ta fad'i hakan had'e da had'iye wani abu me d'aci a zuciyarta. Kaya take sauyawa zuwa na bacci, tana yi tana sakin murmushin samun kwanciyar hankali, saboda rabuwarsu da Rj kenan yace mata gurin Daddy zaije ya sameshi da maganar auransu. Murd'a kofar da Hidaya tayi ne yasata juyawa har lokacin da murmushi akan fuskarta. "Kizo inji Mommy" Hidaya tace da ita had'e da juyawa ta bar dakin. Saukar maganar Hidayan tare suka zo mata da fad'uwar gaba, jiki a sanyaye ta d'auki hijabinta har k'asa ta sanya ta fice. Tun da ta d'ora idonta akan fuskar Momyn taji gabanta ya fara dukan tara tara bama uku ba. Guri ta samu a kasa ta zauna hade da fadin. "Gani Momy" "Nusrat" "Na'am" Ta fada da rawar murya. "Watakan gargadin da nayi miki bai shiga jikinki ya zauna ba har sai da kika aikata abinda zuciya da ruhinki yake so ko, ban isa nayi miki katanga da shi ba saboda kin rainani kika tsallake kika janyo ra'ayinsa ke ga mara mutummci me kike tak'ama da shi ne?‘’ "Ba ke kika haifeshi ba." Hidaya ta fad'a tana turo baki gaba, Nusrat kuwa k'asa tayi da kanta ba tare da tace komai ba tana saurarar yadda kirjinta yake bugu har ma da zuciyarta a yanzun. "D'ago ki kalleni" Momy tace da ita, a hankali ta cire kanta ta sauke idanuwanta kan Mommy wanda suka d'an sauya kala hade da girkicewa. "Kina tak'ama don bani na haifi Rj ba shiyasa kika tsallake maganata?" girgiza kai tayi hade da fadin "Kiyi hakuri." "Hmmm babu wani hak'uri da zanyi sai dai ki karb'i hukuncinki a yanzu, duk da bani na haifi Rj ba amman na haramta aure tsakaninku, kinga matarshi nan wacce akayi mishi tanadinta jira ake kawai ta gama karatunta amman kikazo kina cusa kanki gareshi har sai da kika sauya mishi tunani gaba daya saboda na dauko rayuwarki daga talauci na tsundumoki cikin daula." Idanuwanta sun kuma kad'awa sunyi jazur sun tara ruwa ruwan da ta kasa rik'eshi har sai da suka zubo ta gefen idanuwanta cikin murya cike da son yin kuka tace. "Wallahi Momy ban son da maganar aure tsakanin Hidaya da Rj ba da bazan bashi damar da ya nema a gareni ba, ba nice na cusa kaina gareshi ba shine ya cuso kansa gaba d'aya cikin rayuwata kuma ba tun yau ba tun ban fahimci mece soyayya ba, da na san da maganarsa da Hidaya da bazan bud'e zuciyata gareshi ba, amman yanzu tabbas lokacin rufeta yayi rufewa ta har abada, amman ina buk'atar komawa gida hakan zaifi shafawa rayuwata lafiya ." "Ni kuma bazai shafa mini lafiya ba, kiyi aure kawai shine kwanciyar hankalina." Cewar Hidaya yayin da Momy tace. "K'warai kuwa Nusrat auranki shi zai tabbatar mana da samuwar Rj a hannun Hidaya, don haka ina me sanar da ke gobe manema auranki zasu zo daga gidan su Ishaq samun nutsuwarki ki mik'a wuya zuwa ga wannan aure idan kuwa kika k'i to tabbas zan wulakanta rayuwarki fiye da yadda kike zato don zan iya sauka akan ko wani mataki don ganin yarinyata ta samu farin ciki da nutsuwa." Wayarta ce tayi k'ara wacce kirane daga Daddy akan suzo ita da Nusrat da Hidaya, gasunan kawai tace tana kashe wayar ta ajiye gami da sauke idonta kan Nusrat wacce kawai ga tanan a zaune ne ta kasa sarrafa k'wak'walwarta hade da zuciyarta. "Ki musa maganar auranki na tabbatar miki da abinda nake nufi, muje falon Daddy yana son ganinmu." Tana fadin haka suka mik'e tare da Hidaya suka nufi k'ofa wanda ya bawa Hibba damar dai daita nutsuwarta a bakin k'ofar kamar a lokacin za ta shigo, a tare suka murd'a kofar suna budewa babu wanda yace da ita komai kallo daya suka yiyyi mata suka huce. A hankali take mik'ewa daga zaunen da take tana jin yadda k'afafuwanta suka yi sanyi, sanyin da ba tayi tunanin zasu dauki nauyin gangar jikinta ba, wani irin kunci da zafi zuciyarta take mata, Tabbas iyaye wata babbar katanga ce ga 'yayansu ta tabbata da ace daya daga cikin mahaifanta na raye da bda irin wannan zancen ake a yanzu ba da babu abinda zai kawota zama cikin gidannan bare har hakan ta faru,da ace tasan irin wannan k'addarar na zaman jiranta to tabbas da ba ta yadda zama ya kawota cikin gidannan ba, sai dai kuma ba ka tara sani ga Ubangiji. Cikin matukar sanyin jiki ta nufi k'ofa za ta fita daga d'akin Hibba na biye da ita da kallon tausayi har za ta fice Hibban tayi saurin fadin. "Yayarmu, kada ki aikata abinda zuciya da ruhinki ba zasu taba samun nutsuwa da shi ba, ki cire tsoro a ranki babu wani abu da zai faru da rayuwarki face abinda alkalamin kaddararki ya rubuta, an dauke alkaluma kuma takaddun sun bushe." Juyowa tayi tana kallon Hibban cike da kwarin guiwar da ta samu, murmushi ta sakar mata hade da fadin. "Thanks" Tana jin Hibban cikin tamkar yadda take jin Yusranta, murmushi itama Hibban ta sakar mata tana jinta tamkar ciki daya suka fito don har ga Allah ta fi jin shakuwa da ita fiye da Hidayan da suka fito ciki daya. RJ ne ya sameshi da maganar yana son Nusrat kuma sunma dai daita junansu, duk da yaji wani iri cikin ransa don har ga Allah yaso hada auransa da Hidaya kuma a yadda yake ganinsu yayi tunanin sun dade da dai daita kansu har yake ta tsimayin Rj in yazo ya sameshi da kanshi, a yanzunma da yazo yayi tunanin akan Hidaya ne ashe akan Nusrat ne sai yanzu yakewa maganarsa ta rannan fashin baki da suna dinner yake cewa tabbas zaiyi kewar girkin Nusrat idan tayi aure, yana jin anya kullum ba gidanta zai dinga zuwa dinner ba, sai Rj in yayi dariya yace watakila ma ta wutashsheka zuwa idan ya kasance a kusa kuke kullum da kai za ta saka sanwa. To maganarsa tana nufin idan shi ya auri Nusrat in kenan, bazai ce bai ji dadin soyayyar Rj da Nusrat inba don itama yana jinta tamkar Hidaya da ya haifa, kuma ya san sun dace da aamun kamilar surika to sai dai kuma kansa ya daure da maganar da suka gama yi da Hidaya yanzu, ga kuma Rj in yace da sanin Nusrat in yazo gurinsa don yanzun nan ma suka rabu wannan dalilin ne yasa ya kira Mommy yace tazo da su gaba d'aya. Daga Mommy har Hidaya sun firgita da jin Rj inne ya samu Daddy da maganar auren Nusrat, amman kuma sai Hidayan ta kafe akan Nusrat ince ta aikota gurin Daddy akan maganar Ishaq don ba ta son Rj ya riga zuwa saboda ba shi zuciyarta take ainihin so ba, a tare RJ da Nusrat suka daga kai suna kallonta wanda taki yadda ta kalli daya daga cikinsu. "Nusrat" Daddy ya kira sunanta ta amsa cikin rawar murya. "Na am" "Mene ne ainihin gaskiya." Kuka kawai ta fashe da shi, wanda yazo mata da karfinsa na gaske kuma ba ya bukatar a tsai da shi a yanzu. "Ga ainihin gaskiya nan, tunda ba'a karya da maganar aure, shi Rj in tun da ba ta sonshi ba sai ya hakura ba, dama aishi Hidaya ce matarsa banda abinka." Cewar momy kenan, yayin da zuciyar Rj take ta mugun tafarfasa jijiyoyin kansa sun fito rada rada, Daddy kuwa yayi shiru cikin nazari yayin da Nusrat kukanta yake kara karfi. "Daddy zan gaya maka ainihin gaskiya" Cewar Hibba da ta d'auke ganinta ga kowa illa Daddy da ta fuskanta, duk da ta tsorata da tsawar da Mommy ta daka mata hade da cewa ta fice ba da ita ake magana ba amman Daddy ya dakatar da ita da fadin yana jinta, tabbas za ta fadi gaskiya ko da kwa Momy za tayi gunduwa da naman jikinta. "Yayarmu ba ta san maganar Ishaq ba Aunty Hidaya ce ta tsara komai, kuma Momy tayi mata gargadi akan ta amshi maganar auran Ishaq in don Aunty Hidaya ta samu Yaa Rj a hannu." "Jeki abinki Hibba, Allah ya yi miki albarka." "Amin Daddy." Ta tashi ta fita tana kuma tsoron haduwarta da Mommy don sai huci take ta Hidaya kuwa me sauki ce. "Tabbas Ridwan na so had'a auranka da Hidaya, don duk a tunanina kun jima da hada kanku ashe ba haka abun yake ba, da Hidaya da Nusrat duk daya na daukesu a gurina, idan naki Nusrat tamkar naki Hidaya ne, don haka zanje na nema maka auran Nusrat insha Allah, kuma ba zaa ja lokaci ba kamar yadda kake so." "Amman banji dadi ba, meyasa Daddy tun tuni ba ka sanar da ni wannan kudirin naka ba?" "Saboda ba na son ku tirsasa zuciyoyinku yin abinda bashi take so ba, don haka kada kasa komai a ranka, duk sona duk kaunata na ganinku inuwa daya da Hidaya idan Allah bai so ba hakan bazai taba faruwa ba." Yana kawowa nan ya kalli Hidaya yace . "Sai ki warware auren da kika so kullawa, don wallahi muddun suka zo gobe to ke zan basu, kuma daga yau kisa a ranki ita soyayya ba'a kwacenta ta dole Allah ne yake dasawa bayinsa ba tare da saninsu ba, da kin mikawa Allah lamuranki kina iya samunsa ta cikin sanyi ba tare da kinsha wahala ba idan har mijinki ne a rubuce bazai taba gogewa ba." Yana kawowa nan ya tashi zai shige bedroom don wani irin zafin Momy yake ji, saboda irin turbar da ta dora 'yarsa akai, Nusrar da kukanta ya fara yin k'asa ta kirashi. "Daddy" Tsayawa yayi yana jiran jin abinda za tace. "Daddy na hak'ura da Yaa Rj na barwa Hidaya, wallahi ban san da maganar aure tsakaninsu ba, kuma ban san tana sonshi ba duk da ban bude zuciyata gareshi ba, Daddy ni me iya sadaukar da komai ce ga Hidaya muddun hakan zai sama mata kwanciyar hankali." Gaba daya ya juyo ta zubawa fuskarta idanu, yana kuma jinta cikin ransa, kafin yace. "Ke da ake so, kinji zaki iya sadaukar mata da shi, amman ita da ita take so ta kasa sadaukar miki sai ma k'okarin cusaki wani guri da take, Hidaya wannan nuni ne gareki, yadda Nusrat ta daukeki ba haka kika dauketa ba, Allah yayi miki albarka Nusrat, tabbas kin samu kyakkyawar tarbiya, amman ina so ki sani aure da ke da Ridwan sai dai in babu shi a rubuce." Yana kawowa nan yayi shigewarsa d'aki. 。。。。。。 Daddy yaje ya nemawa RJ auran Nusrat gurin Baffa Shamsu, ya kuma bashi babu jaa don duk abin na gida ne, a take ya bada kud'in aure suka tsayar da rana bayan sallah babba. Rj gaba d'aya ya kasa gane kan Nusrat don duk ta sauya, kullum cikin kunci da damuwa zaka sameta da yayi magana za tace ita wallahi ta hakura ta barwa Hidaya shi, shi kuma ransa yakan baci da jin kalaminta sai yaga kamar dama can ba son nashi take ba, ita kuwa tsoron abinda zai biyo baya take yi, don yanzu Mommy ko gaisuwarta ba ta amsa haka Hidaya ko kallon inda take ba tayi, duk da nasihar da Daddy ya zaunar da ita yayi mata duk a banza, tana tsoron yadda wannan aure zai tafi ya raba zumunci tun kan a daura shi. Tsakanin Momy da Daddy kuwa babu wani shiri, don tayi mugun shaka da yace Nusrat ta samu tarbiya yana nufin ita ba ta bawa nata yayan tarbiya ba kenan, shiyasa da ya watsar da ita itma ta watsar da shi don tana shirin yadda za ta watsa rayuwar Nusrat ne kawai don diyarta ta samu abinda ta ke so don har ciwo Hidayan ta kwanta bayan ankai kudin Nusrat in. Hibba ce take b'allo mata magun gunanta na ulcer tana bata ta sha, don kwana biyu ulcer ince ta takura mata sosai, a had'e ta bata su gaba daya ta korasu da ruwa ba tare da ta duba ko guda nawa bane don da ta lura za taga da karin guda daya wanda Hidayace ta jefa mata shi a ciki don ta sha su samu plane insu ya tafi dai dai, sun samu Daddy yayi tafiya, sai da Hibba ta bar d'akin sannan Momy ta shigo. " Ki had'a komai naki driver yana jiranki zai mayar da ke gida." Shine abinda tace mata ta juya ta bar d'akin, jiki a sanyaye take had'a dukkan wani abu da ta san nata ne cikin wata k'atuwar akwati da Rj ya bata, tana hadawa kirjinta na dukan tara tara, ko da ta gama had'a kayan nata sai ta nemi wayoyinta babba da karamar ta rasa, har Momy ta dawo tana neman wayar. "Naga dai ba da ita kika zo cikin gidan nan ba, don haka kizo ki shige driver yana jira." Ba tace komai ba ta janyo akwatinta ta shige, amman ta so ko da sim inta ne ta cire don shi take yiwa tunda dama da abinta tazo ba anan ta same shi ba. Idanuwanta ta lumshe bayan dai daituwarta cikin motar driver ya ja suka fara tafiya, kafin wasu zafafan hawaye su biyo kuncinta har lokacin kirjinta yana wani irin bugu don ba ta san me suka shirya mata ba ..... Last free page 09037093702 [4/26, 8:46 PM] Rabi: 31 Sun kusan cin rabin tafiya taji mararta tayi wani irin k'ullewa had'e da murd'a mata, rintse idanuwanta tayi tana jin yadda marar tata ke murd'awa da alamu dai period inta ne ke hanya duk da tayi mamakin zuwansa a wannan lokaci don lokacinta bai k'arasa ba ba tafi sati biyu da gama wancan ba sai dai kawai tayi la'akari da wani zubin yakan canja lokacin zuwansa, fatanta dai har su isa gida bai zo ba gudun kar ta b'aci saboda ba shirin zuwansa tayi ba, sai dai fatanta nata bai ciyu ba suna karya kwanar layinsu taji yayi wani ambaliya ya fito saboda sama da kasa da motar tayi saboda jakin baban gida da suka tsallaka, innalillahi take ambata a cikin ranta tana adduar Allah yasa ba ta bata motar ba don in ta jikinta ne da sauk'i saboda dogon hijabine har k'asa a jikinta kuma copee ne kalar baza ta fito ba sai dai danshi, kuma ba matsala tunda har k'ofar gida za ta sauka. Ko da yayi parking a k'ofar gidan nasu ji tayi tana jin nauyin mik'ewa don yanzu ta riga ta tabbatar tayi rushing sosai, inda Allah ya taimaketa sai ya fita daga cikin motar don fito mata da akwatinta da ke cikin boot, idonta ne ya sauka akan dostar motar tayi saurin janyota kafin ta zira k'afafuwanta waje a hankula ra fita daga cikin motar kana ta d'an durk'uso tana goge gurin da dostar, kana ta saka ruwa ta kuma gogewa sai ta rik'e dostar a hannunta don ba za ta iya ajiye mishi ita a haka ba kuma ba za ta iya wullar da jininta ba har sai ta wanke. Daga nan suka yi sallama da driver ya juya saboda babu yunwa a tattare da shi ko kishirwa duk da abinsa ya taho saboda Momy tace yana ajiyeta ya juyo ko gidan ba ta yadda ya shiga ba. Jan akwatinta tayi ta nufi cikin gidan nasu da duk wani taku da za tayi da bugawar kirjinta yake tafiya wanda ba tasan dalilin hakan ba, da sallama a bakinta ta shiga inda ta tarar da IYa da Baffa Shamsu da Umma a tsaye a babban tsakar gidan sun zubo mata idanuwa wanda hakan yasa zuciyarta wani irin harbawa, kafin sautin maganar Baffa Shamsu ya sauka cikin kwanyarta. "Me kika zo yi mana? tunda abinda kika zab'awa rayuwarki kenan ai sai kiyi gaba don baza kizo ki bata mana sunan gida ba." Yayin da Iya tace. "Banda abinka zuwa tayi ta shafa mana bak'in fentin da ta shafowa kanta, don sunan zuriarmu ya b'aci, inama Malam zai dawo yazo yaga wacce yake kira 'yar baiwa yau ga baiwarnan mun gani a k'asa, baiwar karuwanci ba." Saurin rintse ido Nusrat tayi tana jin saukar kalmarta ta k'arshe tare da sarawar b'arin kanta, kafin Umma tace. "To ai dama ai ba abanza taki yin aure ba, dama jira take ta samu guri ta fito da zallar ainihin abinda take aikatawa, gashinan kuwa mun gani anyi walk'iya ta haska mana, ku kalli k'afarta ga jini nan yana d'igowa da alama cikinne ya fara fita." Wani ululun bakin ciki ne ya kama Baffa Shamsu, yana jin takaici da tsanar abinda Nusrat in ta aikata, banda daga bakin Aunty Maryam yaji to tabbas bazai yarda ba a yadda yasan tsananin tarbiya a gurin Nusrat in da kamun kai, yayin da Iya kuma ke ta rafka salati tana bin jinin da ke diga a kasa da kallo. "Tun kan hannuna ya sauka a jikinki ki kama hanya ki bar gidan nan, duk randa zuciyarki ta tsarkaka zaki iya dawowa amma da sharadin sai na aurar da yata don bazanyi saken da zata kasa auruwa kamar ki ba, wannan shine hukuncin kawai da zan iya yi miki." Cewar Baffa Shamsu Wasu zafafan hawaye ne suka ziraro ta kuncinta tana jin yadda zuciya da ruhinta ke wani irin radadi, radadi mai zafi me huyar fassarawa, karuwanci shine abinda ke yawo cikin kanta kuma ta kasa bashi maauni wanda zai auna ya bata me kalmar ke nufi. "Nifa ban fahimci me kuke magana akai ba, bansan me na aikata ba kumin bayani don Allah yadda zan fahimta." "Mu zaki mayar 'yan iska kidahumai, to anki a miki bayanin, ki bace mini da gani na daina ganin bakar fuskar nan taki me kama da ta 'yan ruwa." Cewar IYa Ido ta k'urawa Iyan kamar a fuskarta za ta karanci amsoshin da take son ji yayin da Iyan ta fara rarumar wani ice da ke gefenta had'e da cewa. "Zaki fice daga cikin gidannan ko sai na karya kasusuwanki, don naga alamun don baa taba fatar jikinki ba ne kika tsaya kina mana taurin kai." "Zan fita, amman don Allah ki barni na fara gyara jikina." "Alqur'an kinyi kad'an, cikin gidan malaman zan bari a wanke jinin shege, sakamakon da za kiyiwa soyayyar da Mallam da Audu suka nuna miki kenan, to ba da Zainabu ba wallahi." "Ki barta ta fara gyara jikin nata mana." Cewar Baffa Shanmsu. "Alqur'an baza ta wanke mana d'an shege ba a gidan nan, idan ta k'ara can gaba koma dandalin karuwanne ta wanke." Meye laifinta ne, me ta aikata musu suka tsaneta?Idan dan son da Rj yake mata ne itace tace ya sota, ko kwa ita ta dauki sonta ta d'ora masa, yanzu wannan laifin har ya kai su tsaneta ya kuma kai matakin da zasu yiwa rayuwarta wannan qullin, qullin da Allah ne kad'ai zai iya fidda ita? Tafiya take tana jan akwatunta zuciyarta bak'ikirin, duk wani bayani tayi musu na cewar ba ta san maganar da suke ba sunk'i fahimta kuma ba ta san da wani yare za tayi musu bayanin da zasu fahimta ba, ba ta da wani zab'i da ya wuce na ficewa daga gidan don Iya ta tsaya kai da fata ko gyara jikin nata ba za ta bari ta shiga tayi ba. Tafiya take ba ta san inda zata dosa ba, ba ta da kowa su d'innan dai sune nata, kuma ga abinda suka yi mata, duk maraici shine ginshik'in da ya kawo rayuwarta a haka ta tabbata da yanzu tana jikin Mamanta wacce ta katangesu daga dukkanin wasu matsaloli, amman gashi k'addara ta kawota bigiren da gidan mahaifinta ma ya gagare ta zama bayan k'azamar kalmar da suke kiranta da shi. Idan tace gidan Auncle Iliya za taje, wani nauyin za taje ta kuma d'ora musu, idan kuma tace cikin gidane to tabbas babu wanda zai iya rikonta a ciki sai dai wuk'a da ta d'auko ta kuma dabawa cikinta, don zasu tambayi dalilin korarta idan ya fasu kuwa sunanta ya riga ya gama b'aci wanda babu me wanketa sai Allahn da ya halicceta, don haka kawai ta mik'i titi tana tafiya ba tare da tasan inda take jefa k'afafuwanta ba, da kuma inda ta dosa ba, ina kuma rayuwa za ta d'auketa ta kaita? [4/26, 8:46 PM] Rabi: 32 A gajiye ya shigo cikin gidan lik'is, tun safe da ya fita sai yanzu da ake magana da sallar isha ya samu kansa sakamakon wani aiki da ya tattare masa guri aya, bashi da wata bukatada ya huce na yin wanka tare da sauke sallar ishar da ta rage masa ya nemi makwanci kuma don wuce gajiyar gaba d'aya, amman kuma sam zuciya da idaniyansa sun kasa hak'uri Nusrat kawai suke da burin fara gani, tun bayan fitarsa da sukayi waya ba su sake yi ba saboda bai samu kansa gaba daya ba a wunin yau din. Kansa tsaye cikin gidan ya nufa yana fatan ya sameta a falo ko daga nesa ne ya kalleta zuciyarsa ta samu nutsuwa ya juyo ba tare da magana ta shiga tsakaninsu ba, sai dai kuma Hibba kawai ya tadda a falon tana mutumin nata, sannu da zuwa tayi masa da ka ya amsa mata kafin yace tayi masa magana da Nusrat sai cewa tayi. "Wallahi Yaa tun dawowata daga islamiya nake mata nocking don na kuma duba jikin nata amman shiru ba ta bud'e ba, to nayi tunanin ko bacci take shine na rabu da ita, to yanzu zamana kenan na gama nocking in shiru, naiwa Aunty Hidaya don naji ko lafiya sai tace mini tana toilet Momy kuma da naje sallah take, shine nake jiran idarwarta naji ko lafiya" "To Allah yasa lafiya, jeki ko ta idar, sai ki taho da safayar makullin dakin a bud'e a gani" Ya fad'a da gajiya cikin muryarsa da ta had'e da fargaba da tashin hankali, ko da Hibba ta koma dakin sai ta tarar Mommyn ba ta idar ba don haka ta d'ebo safayar mak'ullan gaba aya da ke cikin drower gado don ba ta san wanne ne daga ciki ba, tunda ba fiya amfani akai da dakin ba sai yanzu da Nusrat in ta zauna bayan sun raba daki da Hidaya. Da Allah ya taimakesu suna gwada maullli na uku sai d'akin ya bud'e, wayam d'akin ba kowa a cikinsa, duk da kirjinsa da ke bugawa amman sai ya bawa kansa k'warin guiwar cewa Hibba. "Kiyi knocking a toilet ko tana ciki." Itama dama tunanin da take kenan don haka ta karasa bakin kofar toilet in tana nocking, tayi kusan sau uku amman shiru don haka kawai ta bud'e, nan dinma dai babu kowa a ciki, ban dakin ma a bushe yake da alamu an jima baa shiga cikinsa ba. "Yaa ba ta ciki." lumshe gajiyayyun idanuwansa kawai yayi, yayin da ita kuma idonta ya sauka kan wata farar takadda da ke kan drower gado da sassarfa ta isa gurin takaddar had'e da wareta gaba aya. "Yaa RJ shine a farkon layin rubutun don haka tayi saurin janye idonta hade da mika masa, har lokacin idanuwansa a lumshe suke don haka sai da ta hada da cewar. "Yaa ga takadda ta bar maka." "Fad'i meye a ciki" Ya fada ba tare da ya bude idanuwansa ba. "Yaa Rj kayi hak'uri bazan iya auranka ba saboda bani da kima da darajar da ko wace mace ke bawa mijinta, Ishaq ne ya cuceni yaci amanata ya b'atan rayuwa, ciwon da na kwanta nace muku ulcer ce to ba ulcer bace laulayin ciki nake, tun da na tabbatar da ciki nake dauke da shi naji bazan iya hada ido da kai ba da Aunty Maryam da Daddy don haka kawai na yanke shawarar barin gidan tun kafin ku gano tab'ar gazar da na aikata, don Allah ku gafarce ni." NUSRAT Bazai ce ga yadda akai ya kawo kansa d'aki ba kawai dai ya tsinci kansa ne a ciki, kayan jikinsa kawai ya tub'e ya fada toilet hade da sakarwa kansa ruwan d'umi ya dade ruwan yana sauka a kansa kafin yayi wanka da d'auro alwala, yana gabatar da sallar ya fad'a gado a rigin gine, duk yadda yakai ga buk'atar sanyawa cikinsa wani abu, ji yayi bakinsa bazai iya karb'a ba bare har ya kaiwa cikin a yadda yake jin ransa gaba aya a jagule, zuciya da k'wak'walwarsa gaba aya a cunkushe suke ya rasa wani irin tunani ma zaiyi abu d'aya ne dai kawai ya san Nusrat ba za ta tab'a aikata abinda ta rubuta ba, ko ma dai meye yana son ji daga bakinta don haka tun asuba zai d'auki hanyar zariya yanzunma don dare yayi ne. Gurin Momy Hibba ta nufa da takaddar a hannunta, takaddar kawai ta bata ba tare da tace komai ba. Momy na gama karantawa ta hau tafa hannu da sallallami kafin tace. "Dama sai da jikina ya bani babu yadda baayi da ita ba aje asibiti tak'i yadda ta kafe akan ulcer inta ce ta tashi a siyo mata magani kawai, aini yadda naga tana ta tashin zuciyar nan da amai ta kuma cinye goron d'ari nasan akwai bayani, ashe cutarmu 'yarnan tayi cikin shege ta yo mana a cikin zuriarmu, Innalillahi wa inna ilaihirrajiun." Sai ta fashe da kuka yayin da Hidaya ta fito tana tambayar abinda ya faru Mommyn tana gaya mata, Hibba dai zare jikinta tayi ta bar d'akin sam ba ta yadda da wannan zancen ba, ta tabbata ba haka zancen yake ba, ita damuwarta ma ina Nusrat in ta tafi fatanta dai Allah yasa tana zariya sai aji komai daga bakinta." Daa da yadda zaiyi ya cire son Nusrat daga zuciyarsa da yayi, saboda zargin da yake tayi hakanne kawai don gujewa auransa saboda ya auri Hidaya, idan sonshi ta daina yi ai ba sai ta shafawa kanta bak'in fentin da ba ya kankaruwa a jikin mutum. Memakon yaji son nata na raguwa sai dai ma dad'uwa da yaji yana yi burin idaniyanshi kawai ya saukesu a kanta. Yana idar da sallar asuba kamar yadda ya k'udurce a ransa ya d'auki hanyar zariya, sai dai zancen da ya samu daga bakin Baffa Shamsu duk ya gama dagula masa lissafi, har yanzu zuciyarsa ba ta gasgata abinda ake zargin Nusrat in da shi ba, shi babban tashin hankalinsa ma da aka koreta, ina ta nufa ina taje duk bai sani ba kuma bai san wanda zai sanar da shi ba, Yusra ce ta fad'o masa a rai don haka ya lalibo numberta ya danna mata kira. "Yaa Rj kai nake lalibowa zan kira ka had'ani da Yayarmu tun jiya nake kiranta ban sameta ba." Maganar Yusra ta sauka cikin kunnuwansa rintse idanuwansa yayi yana jin yadda kansa yayi wani mugun sarawa, ji yayi bazai iya yi mata magana cikin halin da yake ciki ba don haka kawai ya kashe wayar gaba d'aya. 。。。。。。。 Ko ina ta samu jefa k'afafuwanta take saboda yadda k'arfinta gaba d'aya ya k'are gashi dama ba ishashshiyar lafiya gareta ba, ga kuma b'acin rai da cunkushewar zuciya, da kuma tunanin rasa makoma, akwatin nata ji tayi kamar ta wullar saboda yadda yayi mata nauyi ta gaji da jansa, sai dai akwai abubuwanta masu matuk'ar muhinmanci a ciki, tun tana iya taka k'afar tata har ta kai ta kasa d'agata ma, ga hadari da ya had'o yayi murtuk gari yayi bak'ik'k'irin dama magariba ta kawo kai da alamu sallar yake jira ruwa ya sakko gaba aya, gabas yamma kudu arewa duk ta duba ba ta hango wata mafaka da za ta fake ba kafin saukowar ruwan, don haka ba ta da wani zab'i da ya huce zama a gefen titin don k'arfinta ya k'are har ankai matakin da k'afafuwanta ba zasu iya d'aukar gangar jikinta ba. Ana idar da sallar magariba kuwa ruwa ya kece kamar da bakin k'warya, har sai da Isha ta gabato kana ya fara tsagaitawa, wanda gaba d'ayansa ruwan akan Nusrat ya sauka kuma ruwan har da k'ank'ara, ta fice gaba d'aya daga hayyacinta numfashinta sai sama yake da k'asa daga k'arshe ta tsaya cak da aiki.... [4/26, 8:46 PM] Rabi: 33 Motoci ne farare k'al guda uku a jere sai zabga uban gudu suke akan titi kamar zasu tashi sama, har sun gota gurin da Nusrat ke yashe ba ta da maraba da gawa motar da ke tsakiya tayi ribas ta dawo, a dai dai gurin da Nusrat ke yashe dreban yayi parking, yana fitowa a hanzarce rik'e da lema a hannunsa, sai dai ya tarar har ogan nasu ya fito ya nufi gurin da Nusrat ke yashe ga mamakinsa sai gani yayi yasa hannu ya ciccib'ota sai yayi saurin bud'e masa murfin motar ya sakata a ciki, sai jin saukar dakakkiyar muryarsa yayi cikin kunnuwansa yace. "Ka saka akwatin cikin boot." daga haka ya nufi gaban motar ya bude barin da ke zaman banza ya shiga saboda babu space in da zai zauna a bayan duk ta cikeshi. Asibiti direct suka nufa da ita wanda sina zuwa aka karb'eta aka shiga bata taimakon gaggawa, sai da suka ga komai ya dai daita kana suka baro asibitin. Tun kafin isowar motocin nasu securityn da ke bakin babban get in sun wangale musu, suna jiran k'arasowarsu, a guje a kuma jere suka shige suka d'auki titi d'od'ar kafin su tsaya a wani plat mension da ya gaji da matuk'ar had'uwa, ko da suka yi parking a harabar ajiye motocin babu wanda yayi yunk'urin fitowa ganin ogan nasu har lokacin bai fito ba, don drivern da ya tuk'oshi yana parking ya zaga side in da yake ya bud'e mishi k'ofa yana jiran fitowar tasa wanda sai da ya gama shan k'amshin shi kana ya fito ganin haka yasa yaransa sukayi saurin fitowa had'e da take mishi baya har zuwa asalin k'ofar da za ta sadashi da asalin cikin gidan kana suka jaa birki har sai da ya danna code jikin k'ofar ta bud'e ya shige kana suka juya kowa ya tafi yin uzurin gabansa. Falo ne k'ayatacce wanda aka cikashi da dukkannin wani kayan k'awa na duniya, Baba Azumi ce kawai a falon, itama abincinsa ta had'o a babban tray za ta kai masa. "Sannu da zuwa d'an uwana." "Yauwa Baba sannu da k'ok'ari, sai dai yau ba na buk'atar abinci tea kawai zaki taimaka mini da shi me yaji." "An gama d'an uwana." Ta fad'i hakan tana k'ok'arin juyawa yace. "Amm Baba Hadiza taje parking space Khalil yana jiranta." "Insha Allah zan isar da sak'onka." Kai kawai ya jinjina mata had'e da nufar b'arin dama inda zai sadashi da sashensa, falo ne k'awatacce wanda yafi na farkon k'awa sai dai shi wannan babu hayaniya a cikinsa, akwai dining area da 2 bed rooms a ciki, d'aya daga cikin bedroom in ya nufa wanda da shi kawai yake amfani, komai na ciki jajaye ne saboda kalar da yake auna kenan, kayan jikinsa ya tub'e had'e da shigewa toilet ya had'a ruwan wanka ya shige ciki kafin ya lumshe kyawawan idanuwansa wanda suke d'auke da dogayen eye lashers zara zara. Tea in da Baba Azumi ta kawo masa yake sha a hankula yana lumshe idanuwansa, wayarsa da ke gefensa ce tayi k'ara a hankali ya sauke idonsa kan wayar, Bro Asghar shine abinda ke yaho akan secring in wayar d'auke idonsa yayi daga kai yaci gaba da sipping tea insa sai da yayi mishi miss call uku a jere ba tare da yayi peking ba, sai kuma wata wayar ta shigo da ban shima sai a miss call na biyu kana idonsa ya sauka yaga ba na farkon bane wannan Bro Asad ne, dole ya d'aga wayarshi don ya tabbata yau a yadda yake jinsa idan ba da taimakonsa ba bazai iya rintsawa ba, yana peking in wayar bai tsaya saurarar me zaice ba yace. "Ka shigo." A takaice kana ya ajiye wayar ya mayar da idanuwansa ya rufe. Wani shegen murmushi Aasad ya saki yana kallon Asghar kafin yace. "Ko a yanzu ka tabbatar na fika muhimmanci a gurunsa, don haka abinda yafi sauk'i ka ja jiki a gurin da baka da kwarjini, ka kuma daina yunk'urin kub'utar da Damisan da ya dad'e da aminta da zaki, don baza ku tab'a jituwa ba idan har kana kawo sukar zaki a gare shi har abada, idan nace har abada ina nufin har abadan abadina." Yana kawowa nan yasa kai zai huce yayin da Asghar ya sanya hannu a kafad'arsa had'e da fad'in. "Magana d'aya zan gaya maka, domin bani da lokacin da zan tsaya ina musayar magana da kai, ina so ka dinga tunawa da kalmar nan ta hausawa da kan cewa, rana dubu ta b'arawo rana aya tak ta me kaya idan ka isa ka hana wannan ranar zuwa." Yana kawowa nan ya shige cikin motarsa had'e sa yin revers ya fice daga cikin gidan yayin da Aasad yayi wani shu'umin murmushi a ransa yace. "Idan ma rana ayan za ta zo to na tabbata sai ta tab'a zuciyarka domin za kaga abinda zatonka bai tab'a zata ba." 。。。。。。 Lafiya ta gagari Rj har sai da ta dangana shi da asibiti, kwanansa biyu a asibiti Daddy ya dawo, inda yaji labarin komai daga bakin Momy, shi kanshi abin ya matuk'ar d'aure masa kai sam bai yadda Nusrat za ta aikata haka ba, amman dai yayi musu shiru yaja Hibba ba tare da kowa ya sani ba suka tattauna akan lamarin, inda Hibba sam ta nuna itama ba ta yadda musamman rubutun da Nusrat in ta bari ba nata bane don ta tab'a taya Hibban wani note da ta d'auko ta had'a sam basu zo aya ba. Ishaq Daddy ya nema, inda ya saka Hibba sato numbersa a wayar Hidaya, da haka ya sameshi har suka tattauna, shima dai ya nuna bai san da wannan zancan ba ko kad'an, shi tun fara alakarsu da Nusrat ko farcanta bai taba k'ok'arin rik'ewa ba inama yaga fuskar yin hakan. Satin RJ biyu a asibiti aka sallameshi ya d'an fara samun sauk'i, sai dai abinda yake cikin zuciyarsa ne sai Allah kuma, Daddy yana ta tausarsa da kwantar masa da hankali na cewar ya saka a nemo Nusrat in acan garin zariyan, duk da har yau dai babu wani labari nata da aka samu, ya dai d'ora alhakin komai akan Momy, don ya gaya mata duk abinda ya samu Nusrat in hakk'in ya rataya a wuyanta, idanma tayi hakanne don Hidaya ta auri RJ in to ya haramta aure tsakaninsu, ko bayan ransa bai yadda RJ in ya auri Hidaya ba ko da kuwa za ta rasa ranta ne saboda son da take masa zai bar ma wasiyya a rubuce, wannan shine hukuncin da suka sanya zuk'atan marayun Allah a ciki, kafin su karb'i hukuncinsu gurin Ubangiji kuma, duk da rantsuwar da sukai na babu hannunsu cikin lamarin amman sam Daddy bai yadda ba, cikin kwana biyu tak Hidaya ta fara d'and'anar zafin rashin masoyi, zuciyarta ta shiga k'unci da zafi da rad'ad in da ta Rj da Nusrat take ciki, tun da ta riga ta aminta babu aure tsakaninta da RJ in duk yak'in da suka yi ya tashi a banza kenan a take nadama ta fara nuk'urk'usar zuciyarta . (Hhhh yadai Hidaya nadama da wurwuri haka?) A b'angaran Yusra kuwa sam ba ta cikin kwanciyar hankali, don da ta kira Hidaya ta zayyana mata abinda ya faru, ba tayi k'asa a guiwar zuwa gidansu ba hankali a tashe, nanma Iya ta zayyana mata komai, tun daga can take kuka tana ita sam ba ta yadda da wannan sharrin da aka k'agawa Yayarsu ba, saboda su marayu ne babu idon iyayansu shiyasa babu bincike babu komai zaa kama a koreta, Allahn da ya halicceta yana gani kuma zai tallafeta idan ma anso ta lalace ne zai kareta daga haka insha Allah. Kullum cikin kuka take tare da kaiwa Allah kukanta akan ya kare mata yayarta a duk inda take... [4/26, 8:46 PM] Rabi: 34 A hankali idanuwanta suke bud'uwa har suka bud'e gaba d'aya, akan fankar da ke tsaye cak ba ta aiki, sabili da ruwan saman da aka tafka jiya da daddare shiyasa aka tashi garin yau da sanyi, GOGEL HOSPITAL shine abinda ke jikin fankar, wani sanyin dadi taji a ranta sabili kuwa ta san tabbas yau za ta bak'unci lahira, ita kuwa tafi buk'atar hakan a yanzun sama da komai don tana son ta huta sosai. "Alhmdlillh, na godewa wanda ya kawoni asibitin k 'arasani, me likitan yake har yanzu bai k'arasar da ni ba ne? Ku kirashi don Allah ya k'arasani." Takai k'arshen maganar had'e da fashewa da matsanancin kuka, tsorata sosai Baba Hadiza tayi, don a tunaninta ko dai mahaukaciya ce, don haka ta juya kirawo likitan sai ta tadda su shi da likitan sun nufo d'akin don haka tun a hanya take basu labarin abinda ta farka da shi. Ta tashi daga kwancen da take ta had'a kai da guiwa tana ta gurshek'an kuka, shi kuwa ya tafi tunanin ina yasan wannan sautin kukan, sautin da ya zauna cikin kwanyarshi daram, saukar sautin muryarta ya kuma ji da takewa likitan magana yayin da yake duddubata. "Dan Allah na rok'eka ka k'arasani, na gaji da duniyarnan ina so na huta." "Mu ai bama kisa, kuma baza mu fara ta kanki ba, tunda ranku ba'a hannunmu yake ba. " "Mahaifina fa?" "Mahaifinki ya,mutu a nan ne?" Gyad'a mishi kai tayi, yayin da shi kuma yace. "To kwanansa ne ya k'are." "Amma ai ana baku kwangilar kashe mutane ko?" Gabansa ne ya fad'i, a tare tsoro da rud'u ya bayyana akan fuskarsa , yayi saurin kallon gurin da Aashiq yake a tsaye yayi folding hand insa had'e da zubawa fuskarta kyawawan idanuwansa, fuskar da ta zauna cikinsu tun ranar farko da ya fara d'orasu a kanta. Da sauri likitan ya janye idonsa daga kansa ya mayar kanta, yana me addu'ar Allah yasa bai ji abinda ta fad'a ba. "Inma ba kwa karb'ar kwangilar to ni yau na baku ku k'arasani na huta don Allah." Wata wawiyar ajiyar zuciya ya sauke a b'oye kana yace mata. "Ke musulma ce?" Gyad'a mishi kai tayi." "Idan har ke musulma ce kin kuma yadda da k'addara to don me yasa zaki buk'aci mutuwa, bayan mutuwar ba a hannunmu take ba?" "Na yadda da k'addara, don da ban yadda da ita ba titi zanje na kwanta mota tabi ta kaina, zafi da rad'ad'i nake ji a k'irjina, ina so na daina jinsa, baza ka gane ka kuma fuskanci yadda nake ji ba, da ace Mama da Baba suna nan sune zasu fi fuskantata." Sai ta fashe da wani matsanancin kukan, yayin da Aashiq ya kalli Baba Hadiza ba tare da yace uffan ba kuma ta fahimci yaren da yayi mata, kana ya kalli likitan yayi mishi inkiya da suje kawai. Kuka take sosai, yayin da Baba Hadiza ta shiga bata baki had'e da yi mata wa'azi, a hankula cikin hikima take hilyatarta har sai da ta zayyana mata abinda yake faruwa da rayuwarta , saboda yadda da taji tayi da matar tun a kallo d'aya da tayi mata, kafin ta tambayeta ya akai aka kawota asibiti, ita kuma ta sanar mata da cewar KATANGARSU ne ya kawota kuma ya umarci idan ta aminta su tafi gida da ita, babu inda zata je ba kuma ta san inda zata nufa ba don haka ba ta da wani zab'i da ya wuce ta bisu kafin taga yadda Ubangiji zaiyi da rayuwarta don ba ta san k'addarar da ke jiranta a gaba ba. Sallama likitan ya rubuta musu, Khalil ya d'aukesu ya nufi gida da su, tayi mamakin ganin sun nufi GRA sai kuma taga sun shiga gogel estate ta kalli Baba Hadiza tana son jin wani abu daga gareta anman ba tace mata kpmai ba don haka itama ta kama bakinta tayi shiru. Har zasu shige ciki, bayan sun danna door bell Baba Azumi ta bud'e musu, sai Khalil ya tsayar da su, ya basu akwatin Nusrat in, tayi matuk'ar farin cikin ganin akwatin nata don daa har ta saddak'ar ya salwanta. Fuska sake Baba Azumi ta tareta yayin da itama ta gaisheta cike da fara'a don ji tayi matar ta burgeta ta kuma shiga ranta sosai da sosai, D'aki Baba Hadiza ta kaita ta nuna mata toilet. Wanka tayi sosai ta gasa jikinta, tayi mamakin ganin jinin ya d'auke don haka kawai sai tayo wankan tsarki ta fito, sai da ta gama shiryawa kana ta zauna a bakin gado tana sauke idon kan wani hoto da ke manne a bangon d'aki, idan ka cire fuskokin mutum biyunnan da ta gani to babu wanda kuma ta sani, Baba Hadiza ce ta shigo tace ta taso taci abinci sai ta sha magun gunanta. Baba Hadiza ce da kanta tayi sarving nata ta fara cin abincin a hankula kafin suji k'arar door bell, Baba Hadiza ta nufi babban falon don bud'e k'ofar. Yara ne su uku, mata biyu namiji d'aya sai kuma budurwa kamar Yusranta suka shigo, Baba Azumi ce ta kalli 'yar budurwar had'e da fad'in. " Ba dai har an tasheku ba?" Dak'una fuska tayi kafin tace. "Kai Baba duk dad'ewar nan da nake ganin munyi." Takai k'arshen maganar tana sauke idonta kan Nusrat kafin ta kalli Baba Hadiza. "K'aruwa muka samu." Baba Hadiza tace mata, murmushi ta saki had'e da k'arasawa gurin Nusrat in tace. "Sannu Aunty, sunana Fa'iza, nice autar gidannan, wa'yannan yaran da kike gani arosu mukayi nan da anjima zan wulla ko wacce gidansu." "Aunty nice nan auta sunana Aalisha Baby." "Wallahi Aunty nice nan Auta sunana Falisha Beauty." "Ni kuma nine babbansu sunana Yaya Aliyu, Aunty da ni kad'ai zaki dinga zuwa shan ice cream ko duk nafi Aalisha da Faliisha hankali." Murmushi tayi tana jin wani sanyi a ranta had'e da mamakin Yaa Aliyu da alamu Falisha da Aalisha zasu girmeshi amman sai yaci girman yace shine babba tunda su daga jin Faiza tace itace Auta suka ara suka yafa. "Ni kuma sunana Nusrat, naji dad'in kasancewata a cikinku." Takai k'arshen maganar tana sauke idonta kan Faiza. "Muma munji dad'in zuwanki sosai da sosai, bara mu cire uniform." "Godiya nake, a fito lafiya." "Allah yasa Aunty." Daga haka taja hannun su Falisha zuwa ciki." "Haka kuke da karamci?" Ba ta san lokacin da bakinta ya jefowa Baba Hadiza wannan tambayar ba, murmushi Baba Hadiza tayi had'e da fad'in. A kanshi aka rainemu Nusrat dole ne mu kasance muna yinsa. _"A hali na hauka na tsinci kaina daga wannan bola zuwa wannan bola nake rayuwa, babu wanda ya tausaya mini ya kalleni a matsayin yar adam sai shi, shi ya d'aukeni ya kaini asibiti akayi mini magani har na samu kaina, ko da na warke Nusrat ban san ni d'in wace ce ba, ban san komai akan kaina ba, haka ya d'auko ni ya kawoni cikin gidan nan ya bani ci ya bani sha had'e da sutura, ya kuma bani farin ciki, wannan farin cikin sune wannan ahalin_" Takai k'arshen maganar tana ajiye hoto a gabanta window size, kana taci gaba. _Falisha, Nabila, Ramla, Rabi'ah, Farida, Faiza, Baba Azumi, Baba Hadiza ni kenan, sai kuma k'anwarsa uwa d'aya uba d'aya Aalisha._ _Wa'yannan sune farin cikin da Aashiq ya bamu, domin sun d'aukemu ni da Baba Azumi tamkar mu muka tsuguna muka haifesu, mun sosu sun somu, mun k'aunacesu sun k'aunacemu, rayuwa muke me cike da farin ciki da annushuwa, dukkaninmu marayu ne don bamu da kowa ba mu san kowa namu ba, Aashiq shine KATANGARMU domin yayi mana katanga da k'unci da damuwa, da kuma rayuwar k'ask'anci da wulak'ancin da muka taso a cikinta, da badan shi ba da tuni muna can muna garari a cikin duniya amman sai ya had'emu guri d'aya ya bamu farin ciki wato junanmu muka zamo ahali d'aya, wanda har daga k'arshe rik'on k'anwarsa ya dawo hannunmu._ _Faiza 'yar Baba Azumi ce ta cikinta, Nabila, Ramla,Rabi'ah,Farida duk mun aurar da su, Falisha 'yar wajen Rabi'ah ce, Aalisha kuma ta gurin Nabila, Aliyu shi kuma na Farida ne, Ramlah ce ita kuma sai yanzu Allah ya kawo rabon tana goyan 'yan biyu Safa da Marwa._ "Allah ya,biyashi, ya kyautata rayuwarsa kamar yadda ya kyautata tamu gaba d'aya, amman Falisha da Aalisha fa?" Cewar Nusrat kenan yayin da Baba Azumi da Baba Hadiza suka hada baki gurin cewa."Amin ya Allah" Kafin tambayarta ta dakesu, dukkaninsu sai da idanuwansu suka kad'a kafin suce. "Allah yayi musu rasuwa." "Allah yayi musu rahama, kuyi hak'uri" Sam ba taji dad'in yanayin da taga sun shiga ba sai taji dama ba ta tambayesu su ba, ta hak'ura da iya abinda suka sanar mata......[6/8, 6:00 PM] Rabi: 35 Rayuwarta a cikin gidan, rayuwace me matuk'ar dad'i da nishad'i, ta samu kwanciyar hankali had'e da nutsuwar zuciya, don tana matuk'ar jin dad'i da mutane gidan haka suma suna jin dad'in zama da ita, ba su,tab'a samun matsala da kowa ba gashi har ta d'ibi kusan wata guda a cikin gidan. Kowa sonta yake hatta su Rabee'ah da suka zazzo kafin su tafi sai da shak'uwa ta shiga tsakaninsu mai k'arfi Faleesha da Aaleesha kuwa dama sun mak'ale mata ko da yaushe suna tare da ita indai ba makaranta suka je ba. Ta karb'ewa Baba Hadiza da Baba Azumi girki, itace take had'a musu girkuna kala kala masu matuk'ar dad'i, ada Baba Azumi ta sakar mata girkinne don ta san Aashiq ba ya nan, don ba ta son a samu matsala, da kuma taji irin d'an d'anon girkin Nusrat in sai taji ko da ya dawo za ta iya kai mishi, may be ma yafi buk'atar irin d'an d'anon, don d'an d'anon girkin Nusrat in ya tafi da su babu k'arya. Tun a washe garin da tazo gidan ta ari wayar Baba Hadiza ta kira Yusra, farin ciki gurin Yusra ba'a magana don a kwanakin nan Allah ne kad'ai yasan halin da zuciyarta take ciki game da Yayar tasun, ta sanar mata abinda ya faru da ita da kuma inda take zaune a ciki a yanzu, tun a ranar Yusran taso zuwa amman ta dakatar da ita akan ta bari tukunna ba yanzu ba, ba ta so hakan ba kuma tayi niyar gayawa kawu Iliya shima ta haneta don tasan muddun ta gaya mishi to zaice ta dawo gidan nasa da zama kuma nauyin zai mishi yawa don yanzu samun nashi ya d'anja baya ba kamar daa ba. Damuwarta Shukhura da Yaa RJ, har yanzu soyayyar 'yar uwartata tana zaune daram a cikin zuciyarta kullum da mikin rashinta cikin rayuwarsu take kwana take tashi, sai dai ba tayi k'asa a guiwar kaiwa Allah kukanta ba, sam ba ta gajiya kullum da kai mishi buk'atarta tasan kuma zai amsa mata lokaci ne baiyi ba, tana fatan zuwan lokacin da ranta da lafiyarta domin ta samu damar cikawa Mama alk'awarinta a kanta. RJ kuwa damuwarta a kanshi ba tasan wani hali yanzu yake ciki ba, don tayi amannar yana yi mata so ba na wasa ba, rashinta kuwa gareshi bazai shafawa zuciyarsa lafiya ba, amman kullum tana nema musu sauk'i gurin Ubangiji akan ya sassauta musu abinda suke ji cikin zuciyoyinsu game da juna don ta riga ta haramtawa RJ kanta ko da kuwa ya gano inda take a yanzu, duk da da wuya hakanma ta kasance don babu wata k'ofa da zai gano hakan sai dai in idan ita taso hakan. " Nusratt" Taji muryar Baba Hadiza na k'wallo mata kira, amsawa tayi had'e da fitowa daga cikin d'akin da sauri. "Kiranki akeyi kinga har ta ma katse." Takai k'arshen maganar had'e da mik'o mata wayar, ba ta kai ga yin magana ba wani kiran ya kuma shigowa, don haka tayi saurin yin peking. "Yayarmu gani a bakin estate in." "Innalillahi, me yasa Yusra ba kya jin magana ne? Nace ki bari ni zanzo gurinki, yanzu ya kike so nayi miki?" "Yi hak'uri Yayarmu, wallahi na kasa samun nutsuwar zuciya ne." Numfashi ta ajiye, had'e da jin Yusran sosai cikin ranta kafin tace. "Bara na gwada na gani ko zaki iya shigowa." Ba ta jirayi me zata ce ba ta sauke wayar daga kunnenta had'e da kallon Baba Hadiza tace. "K'anwata ce tazo, ko da taimakon da za'a mun ta samu shigowa?" "Too, bari dai na gayawa Baba Azumi sai ta sanarwa da Aashiq in." A kitchen ta tadda Baba Azumin ta sanar mata ita kuma ta d'auki waya ta kirashi sabili da ba ko yaushe yake so a shigo masa sashen nasa ba dama Baba Azumin ce kawai me shiga saboda kai masa abinci shima iyakarta falo kawai. Tana gaya mishi yace. "Khalil zaiji da komai. Don haka ta koma ta gayawa Baba Hadizan ita kuma ta sanarwa da Nusrat in, dama duk ta k'agu taji Yusran za ta iya shigowa in ba za ta iya shigowa ba to ita tabbas za taje ta sameta. Tsakanin ita da Yusran ba zan iya tantance muku wanda yafi wani murna ba, sai bayan sun gama zumudin ganin juna kana Yusra ta d'auko wani d'an madai daicin plas tana k'ok'arin bud'ewa tace. "Masoyiya yau Aunty Hafsa tayi mana tayi mugun dad'i aikwa nace sai na kawo miki." "Wake da shinkafa?" Cewar Nusrat, kafin Yusran tace. "A'a d'aya masoyiyar" "Awara" Cewar Nusrat tana dariya yayin da Yusran ma tayi dariya had'e da mik'a mata plas in, hannunta har rawa yake yi gurin aukar guda aya takai bakinta had'e da lumshe idanuwanta. "Allah ya yi miki albarka Yusra, kin matuk'ar sanyani farin ciki, kinsan rabon da naci awara tun da na baro gidan Aunty Maryam, Allah ya jik'an Daddy ba don ya mutu ba, tun da ya san ina son awara kullum sai ya taho min da ita, ban san a ina yake siyowa ba amman sun iya, jabar jabar za ki ganta da k'wai a jiki gwanin dad'i. "Allah sarki Daddy, ai wallahi yana matuk'ar sonki." "Kedai bari Yusra, ba a cewa komai. Baba Hadiza Baba Azumi ga awara don za ku iya ganin plas." Dariya Baba Azumi tayi had'e da cewa. "Ai ba kice kina son awara ba da kwa nayi miki tun zuwanki Nusrat." "Yo Baba Azumi na ganku a cikin uwar daular nan ina zanyi tunanin kunsan wata aba awara, bare kuma yadda ake yinta?" "Ni kwa na iya awara 'yarnan idan na miki awara sai kunnanki ya cire don dad'i, sana'ata kenan a daa" Tsalle tayi daga zaunan da take had'e da fad'in. "Yauwa Baba Azumi shiyasa nake sonki, kiyi mini ta sati na saka pridge nai ta sank'amar kayata." "Idan kin barta tayi satin ba." Cewar Yusra. "Yanzu ta kwano ba za ta iya barinta tayi sati ba?" Fad'in Baba Azumi tana kallon Yusra. "Yayarmu ce fa, Yayarmu da awara kuma ai sai Allah, duk ranar da Mamanmu tayi mana baifi muci uku uku ba duk ita take tashi da ita. Nusrat dai gefe ta ja tana cin awrarta ta bar Yusra da su Baba Azumi suna ta hira. Da fatan munyi sallah lafiya, Allah ya karbi ibadunmu yasa muna da rabon ganin wasu shekarun cikin k'oshin lafiya Allahuma amin [6/8, 6:00 PM] Rabi: 36 Sai bayan sallar la'asar Yusra ta tashi tafiya Nusrat ta yo mata rakiya, sunzo babban falo wani sihirtaccen k'amshi ya ziyarci hancinansu a hankula Nusrat ta ciri kanta had'e da d'orawa gurin da k'amshin ke sirarowa idanuwanta . A hankula yake takunsa cikin nutsuwa da kamewa, idanuwansa akan Nusrat ya fara sauka don haka suka gauraya guri d'aya da nata, rabon da ya sanyata cikin idanuwansa tun a asibiti, don sam ba ya son alak'arta da idanuwansa duk da har yau tak'i barin cikinsu amman idan ba su ganta ba yakan ji sauk'in abun. Ba ta tantance wanda ya taimaketa har take zaune a k'ark'ashinsa ba sai a yau d'in, ba ta mance fuskarsa ba shine wannan kyakkyawan da sukayi arangama da shi har sau biyu a asibitin gogel. A lokaci guda duk suka zare idanuwansu daga na juna amman ita akan bak'in sandan da ke hannunsa ta sauke idonta, shi kanshi sandan abin kallo ne abin kuma burgewa don da ganinsa kasan zaiyi matuk'ar tsada. Yusra ce da ta ankara da fitowarsa tayi saurin tsugunawa had'e da fad'in. "Ina yini" Ko gurin da take bai kalla ba yasa kai had'e da bud'e k'ofar ya fice. Wani k'ululin bak'in ciki ne ya kamata ta sauke idonta akan Nusrat tana mata kallon tambayar. "Dama haka yake?" "Nima ban sani ba Yusra, ko damar yi masa godiya nima ban samu ba, tun zamana a gidan wannan ne karona na farko da na ganshi, amman da alamunsa zaiyi jin kai." Nusrat tace da ita haka, jinjina kai kawai tayi suka saka kai suka fice. Yana k'ok'arin shiga mota yaji an k'walla masa kira. "Yayaa" Cak ya tsaya daga k'ok'arin shiga motar da yake, domin ji yayi tamkar muryar Aaleesha duk da yasan gizo ne kawai na kunnuwansa domin kuwa ta riga tayi tafiyar da babu dawowa a cikinta, waigawa yayi don ganin me kirann nasa, akan Yusra idanuwansa suka sauka dake had'owa da sassarfa don tayi saurin cimmasa, idan ba gizo irin na idanuwansa ba ma sai yaga har d'iban kamanni suke da Aaleeshan. Gurin da yake ta nufa kai tsaye had'e da tsugunawa tana 'yan dube dube kamar me neman wani abu, idan ya,matsa sai ta matso tana duba har tsakiyar k'afafuwansa, cikin kamammiyar muryarsa yace. "Ke lafiyanki kuwa?" Don daa har yaransa sun harzuk'a sun yo kanta, kallo d'aya yayi musu suka koma yadda suke. "Lafiyana qalau, murmushinka kawai nake nema ko Allah xai bani sa'ar laliboshi a duk inda ka b'oyeshi." Wani bazataccen murmushi ne ya sauka akan kyakkyawar fuskarsa, wanda gaba d'aya yaransa suka saki baki suna kallon ikon Allah, har da Asghar wanda tare ma zasu fita ya fito daga cikin motar yana ganin ikon Allah, rabon da irin wannan murmushin ya sauka akan fuskarsa tun kafin mutuwar Aaleesha ne. "Ko kai fa wallahi har ka k'ara kyau sai naga zubin dimple inka kamar irin na Yayarmu, Yayarmu yi murmushi mu gani." Takai k'arshen maganar tana waigowa gurin da Nusrat in ke tsaye tana kallon ikon Allah, wanda shi kuma Aashiq hakan ya bashi damar shigewa cikin mota ya zauna." "Ai ban gama da kai ba, ni sunana Yusra k'anwar Nusrat ce uwa aya uba aya, duk duniya idan ka cire iyayan da suka kawomu duniya to bani da tamkarta, ina sonta ina kuma son duk wanda ya sota, duk wanda ya k'aunaceta tamkar ni ya k'aunata, da ba dan ka ceci rayuwarta ba da bai zama lallai na kuma d'ora idanuwana a kanta ba wanda ban san halin da zuciyata za ta kasance ba kuma, na gode godiya wacce bakina bazai iya fad'in adadinta ba, Allah ya saka maka da gidan aljanna, ya duba gabanka da bayanka ya kuma shiga cikin lamarin rayuwarka. "Amin,thanks" Yace da ita yana k'ok'arin rufe motar, duk da a ransa yarinyar ta matuk'ar burgeshi saboda k'aunar da takewa 'yar uwarta. "Ba ka gaya mini sunanka ba" Rintse idanuwansa yayi don ya fara gajiya, rabon da yayi doguwar magana irin haka har ya manta lokacin, a gajarce yace da ita. "Aashiq" "Nice name, kana k'anwa da ni?" Jinjina mata kai yayi " Thanks, yanzu bari na shiga motar na biku, don ka gayawa wa'yannan k'artin securityn ni k'anwarka ce yanzu bani da KATANGA da estate innan duk sanda na so shigota." Gurin da Khalil yake a tsaye kawai ya kalla, yayi saurin zuwa gurin da Yusran ke tsaye had'e da fad'in. "Ki shiga waccan motar, nine zan kaiki har gida." Yakai k'arshen maganar yana nuna mata motar. "Thanks Yayanmu." Duk da a lokacin ma Asghar ya riga ya ja motar zasu fice. Nusrat cewa tayi za tabi Khalil in suje su ajiye Yusran a gida, bai hanata ba yace ta shigo suje in, suka shiga tana tayiwa Yusra fad'an zaro zance kamar wata babbar mace, don yau ta k'ure lissafin Nusrat in, don ko ita ba za ta iya zaro maganganun da tayi a yanzun ba duk da maganar tata cikin hikima tayita da wayo da basira yanzun ma cewa tayi. "Yayarmu kiyi hak'uri, matsayinki a zuciyata yayi nisan da baki bazai iya fad'arsa ba, hakanne yasa nake ganin girma da kimar duk wanda ya girmamaki, k'anwar mahaifinmu tayi miki tuggun da k'anin mahaifinmu da kakarmu su kaki amsarki, shine ya taimakeki ya ceto rayuwarki ta hanyar kaiki asibiti, sannan ya baki matsuguni me kyau ba tare da yasan ke d'in wace ce ba, daga kuma ina kika fito, a zahirin gaskiya wannan abin da yayi miki yasa kimarsa da mutuncinsa baza su tab'a barin idanuwana, ina kuma jin sonshi tamkar Babban Yayanmu, tabbas da ace a gidan nake a zaune to zan sauyashi zan kuma dawo da murmushi akan fuskarsa." Sai da khalil in ya tsaya a bakin babban get in yayiwa securityn bayanin Yusran kana suka fice tana gaya mishi unguwar da zasu je. "Wace ce wannan yarinyar?" Cewar Asghar yana juyo da kallonsa ga Aashiq in don jiran jin amsar da zai bashi. "Nima ba nace ba, yayarta ce ke zaune a nan gidan." Mayar da kansa yayi ga tuk'in da yake, duk da a cikin estate in suke ba wani guri zasu fita ba, don ya san daga haka bazai kuma d'ora komai ba ko da kuwa ya kuma jefo masa wata tambayar, don k'aidarsa ce tambaya aya yake amsawa itama kuma a gajarce, shiyasa yau in kowa yayi mamakinsa. Gidan su Aashiq suka fara zuwa wanda mahaifiyar mahaifinsa ce ke zaune a cikin gidan Hajiya Zuwaira wacce suke kira da Hajjaju, macece wacce ba ta fiya son mutane na rab'arta ba idan ba jininta ba, suma d'in ba kowa ba, hakanne yasa take zaune ita kad'ai a cikin gidan sai masu yi mata hidima, sai dai Aashiq in kullum zaizo su gaisa idan bai samu zuwa da safe ba to zai zo da yamma, wani zubin kuma yakan dawo nan d'in da zama sai dai ya dinga lek'awa su Baba Azumi, tana matuk'ar k'aunar jikan nata haka shima yana k'aunar kakar tasa. Sun sameta ba ta jin dad'i guiwoyinta sun matsa mata da ciwo wanda hakan ya d'aga hankalin Aashiq sosai. "Kema Hajjaju kin fiya kafiyane wallahi, ki yadda a fita da ke k'asar waje yadda za'a fi bincikar guiwar taki sosai a gano kan matsalar." "Uhmm uhm nidai Turaki ka barni anan, idan wa'adina ma yazo a binneni a k'asata, don kak'i yadda ne ma ni da gogel zanyi tafiyata a binneni a mahaifata." Baice komai ba saboda kayan takaici da yayi masa yawa sai number Dr Sa'ad da yake kira saboda shine family doctor insu, k'wararran likita ne ya karanci ko wani fanni na likitanci. Ya d'an bata taimako had'e da wasu magun gunan da zai taimaka mata wajen rage zafin ciwon da take ji, kana yayi mata allurar bacci saboda har da zazzab'i a jikinta, ana yi mata allurar ba jimawa bacci ya d'auketa, inda likitan ya buk'aci da kar a barta ita kad'ai a samu wani ya zauna tare da ita, inda ya kira wata daga cikin masu mata hidima ta zauna da ita su kuma suka fito. Tazarar zuwan jinin haihuwa da haila shine: Idan jini haihuwa yazo miki kuma kafin ya cika kwanaki 60 ya auke sannan ya dawo bayan k'asa da kwana 15, hukuncin wannan jinin, jinin haihuwa ne ya dawo miki anan zaki kula sosai ki lissafa kwanakin da kikayi a baya sai ki d'ora da sabon da yazo miki har zuwa kwana 60 iya adadin kwanakin da jinin haihuwaa ke daauka yana zuwa. Idan kuma bayan kwana 15 ko sama da haka ya dawo miki to hukuncin wannan jinin jinin haila ne yazo miki wato kin fita daga jinin haihuwa. Abin lura anan shine tazarar jinin haihuwa da haila shine kwanaki 15, idan bai kai haka ba to jinin haihuwa ne ya dawo idan kuma yakai kwanaki 15 ko sama da haka jinin haila ne yazo. Allah ne mafi sani. [6/8, 6:01 PM] Rabi: 37 Gidan su Asghar suka shiga wanda yake jikin na su Aashiq in, inda mahaifiyar Asghar in Hajja tayiwa Aashiq in tarba ta mutumci kamar ko da yaushe idan ya shigo gidan, ba su samu Baffa mahaifin Asghar in a gida ba don haka ba su wani jima ba suka fito suka shiga gidan su Aasad wanda shima yake jikin na su Aasghar, sai wani daga jikin d'aya b'angaran shi kuma na Baffa Ibrahim ne, sai dai shi ba ya ciki ya koma can gogel da zama tare da iyalinsa, babu yadda Aashiq bai yi dashi ya dawo ba yak'i, kuma har yau yak'i fad'in dalilinsa na barin estate in, sai dai Aashiq in yakan ziyartarsa akai akai. Mahaifiyar Aasad ma ta musu tarb'a ta mutumci, kamar ko yaushe yadda kasan ta lashe Aashiq in don so da k'auna, sun samu Mahaifin Aasad in Baffa k'arami yana gida, don haka suka zauna suna tattaunawa duk da yawanci maganar da Asgar ne akan companys kafin Baffa k'aramin ya dubi Aashiq yace. "Kai kuma sai yaushe ne zaka shirya yin aiki a companys in mahaifinka ? Duk ka bar mana nauyi akanmu, kuma kasan girma kamamu yake aikin kuma zaiwa Aasad da Asghar yawa nan gaba." "Ban jin akwai lokaci gaskiya, saboda har yau ba na shaawar aikin." "Duk sanda ka shiryawa hakan kujerarka tana nan tana jiranka, amman dai ya kamata ka yiwa kanka fad'a tun da yanzu ba wani aiki kake ba, kawai kana zaune ne." "Babu takura a zaman nawa haka shiyasa." Daga haka suka yi masa sallama suka fito, saboda kiraye kirayen sallah da aka a fara yi, masallaci suka nufa, acan sukayu alwala kana suka shiga cikin masallacin, sai da sukayi sallar isha'i kana suka fito, gidan Asghar in suka nufa wanda yake can cikin estate in,kasancewar Ramla ta riga da tasan da zuwansa tare da Aashiq in tayi masa girkin da ta san yafi k'auna ta jere musu akan dining tana jiran isowarsu cike da zumud'i don ta kwana biyu ba taga Yaa Aashiq in ba don kulle Asghar in yake mata gata a cikin estate in amman sai ta shafe fin wata ba taje gida ba, har su Rabeeah da suke waje sun fita zuwa, da ta kaiwa Aashiq in k'ara sai cewa yayi. "Ai yayi miki da sauk'i, in nine sai bayan wata shida zaki dinga zuwa gida." Tana jin haka taja bakinta ta tsuke don Allah na gani baza ta iya wata shida ba tare da taje gida ba, a hakanma tana jinta a takure don Allah na gani tana kewar su Baba Azumi sosai tare da shi kanshi Aashiq don ba kasafai yake zuwa ba, yau ma Asghar inne ya mata alkawarin janyo mata shi. Suna cikin cin abincin Aashiq yace da Asghar. "Ina tunanin Baba Azumi zan kaiwa Hajjaju ta zauna tare da ita,saboda likita yace a daina barinta ita kad'ai, in yaso nima sai na dawo gidan da zama." "Amman ni a nawa tunanin kai mata Baba Azumi kamar baza ta so hakan ba, kasan Hajjaju ba kowa take so yana rab'arta ba, gashi kuma d'aki d'aya zasu na kwana, gara ka kai mata wannan yarinyar ina ganin kamar za ta fison hakan, may be tasu tazo d'aya." Jinjina kai yayi kafin ya bud'i baki yace. "Zan duba hakan mu gani." Kiran wayar Aasad ne ya shigo wayarsa sai da ta kusa katsewa ya aga, kamar ba jiran kirannasa yake ba don yau babu ko kwalba d'aya a cikin pridge hakana ma cocaine in ba ya jin yana da ragowarta, in kwa babu su yasan babu shi babu bacci a yau d'innan." "Gani na shigo cikin gidan." "Ok, ka bani mintuna goma." Daga haka ya mik'e yana sauke idonsa akan Asghar da yanayinsa ya sauya sosai, baice mishi komai ba ya mayar da idonsa kan Lamra kafin ya furta. "Allah tashemu lafiya." Sai da ya shafa kan twince dake kwance kan gadajansu suna bacci kana ya fice, Asghar na bin bayansa da wani irin kallo yana jin tuk'uk'i da bak'in ciki, tun da yaga kiran daga Aasad ne yasan bazai huce hodar iblis ko giya ya kawo masa ba, yayi mugun tsanar wannan d'abi'ah da ya bud'i ido rana tsaka yaga Aashiq in a ciki dumu dumu, wanda a daa yafi kowa mugun tsanarta, kullum cikin yak'i yake da masu aikatata amman sai da Aasad yasan yadda yayi ya dilmiyar da shi a ciki wanda shi kuma har yau har gobe yake fafutukar ganin ya cirewa Aashiq in sha'awar shan wani abu da ya danganci maye, kuma akan hakanne suke samun sab'ani da shi har Aasad in yayi amfani da wannan damar gurin shiga tsakaninsu. Sai da ya fara biyawa ya duba jikin Hajjaju, har lokacin bacci take, kuma wacce ya sanya ta zauna tare da ita har ta tafi don ba anan suke kwana ba zuwa suke su tafi, don haka ya taho da niyar turo yarinyar nan ta zauna da ita, don sai yaji ya amshi shawarar Asghar in. Ta k'ofar da ta zamto tasa shi kad'ai suka bi, ta nan aka shishshigar masa da d'ima d'iman kwalika ke kyace abin arzik'i ne a ciki, nan kwa giya ce a ciki (Barasar faransa)duk pridge in da ke sashensa aka ciccika su da barasar, kana ya ajiye mishi cocaine in had'e da fad'in. "Kasha ka ji Ashh wannan ba irin sauran bace ta fita da ban, in ka sha biya na musamman zakamun." Ba tare da yace komai ba ya zazzagi hodar a hannunsa ya zuk'a had'e da lumshe idanuwansa. Biya na musamman in kuwa yayi masa kafin suyi sallama ya fice ya kulle k'ofarsa, wanka yake shirin shiga kana ya tuna da aikawa Hajjaju yarinyar nan don haka ya d'auki waya ya kira Baba Azumi ys shaida mata Nusrat in ta had'a kayanta Khalil zai kaita gurin Hajjaju. Duk da a cikin estate inne amman sam Baba Azumi da Baba Hadiza ba suji dad'in rabuwa da Nusrat ba, musamman su da sunsan ba zuwa gidan zasuyi ba sai dai in ita tazo, don k'arara Hajjajun ta fito ta nuna ba ta son suzo gurin da take, kuma ba suji zafinta ba kasancewar Aashiq jikanta, shikuma Aashiq KATANGARSU ne bango majinginarsu baya goya marayu, sunaiwa Nusrat in fatan dacewa da samun jin dad'in zama tare da Hajjajun, ita kanta Nusrat in ba taji dad'in sauya mata gurin zama ba, ta riga ta saki jiki da su Baba Azumi tana mugun jin dad'in zama da su, sai dai babu yadda za ta yi dole ne ta bi umarnin wanda take zaune a k'ark'ashinsa don da ba dan shi ba da k'ila tana can tana garari a duniya. Allah ya taimaka Faleesha da Aleesha bacci suke da mak'alewa zasui sai sun bita, sai dai kwa za'a sha rigima idan suka daina ganinta, Aliyu kuwa dama ya gudu gidansu, su kuwa tunda suka ga Nusrat in suka lik'e mata sukak'i tafiya... Manzon Allah (SAW)yace. "Sai naga wasu mata an rataye su da gashin kansu jikin bishiyar zakumi, kuma ana kwara musu ruwan zafi naman jikinsu yana kwalewa ana dawo musu da halittarsu sabuwa, sai yace su waye wannan ya d'an uwana Jibrilu?" Sai yace. "Sune matan da suke shan k'wayoyin magani don su kashe 'ya'yan dake cikin cikinsu don tsoron ciyarwa ko shayarwa ko tarbiya, shin basu san Allah ne yake ciyar da su ya shayar da su? Hakika Ubangiji ya fad'a cewa,(Babu wata halitta a bayan k'asa face Allah ne yake ciyar da ita.) [6/8, 6:01 PM] Rabi: 38 Man zafi take shafawa Hajjaju akan guiwoyinta bayan ta gama yi mata tofi a kansu, k'arar door bell su kaji, a hankula ta mik'e don zuwa ganin wanda yake neman iso. Bud'ewar k'ofar tare yazo mata da fad'uwar gaba, kafin idanuwanta su shiga cikin nasa, yana tsaye, fuskar nan tasa a kame kamar ko da yaushe sai k'yalli yake yana zuba k'amshi, gefe ta jaa don bashi hanyar hucewa kafin tai k'asa da kanta had'e da fad'in. "Barka da dare" Ko kallon gefen da take bai yi ba yasa kai zuwa ciki dama kuma ba ta saka ran zai amsa mata ba, tana shirin rufe k'ofar sai ga Asghar ya taho, dama tare suke ya d'an tsaya ya amsa waya ne."Barka da dare" Tace masa da murmushi akan fuskarsa ya amsa mata da. "Barkanki dai, da fatan kin huni lafiya?" "Lafiya lau."Ta amsa mishi. A falo ta nemi guri ta zauna tana sauke idanuwanta akan TV duk da kallo ita ba damunta yayi ba wannan sai Shukhura, Hibba ce ta fad'o mata a rai, ta tabbata uanzu in ba'ai sa'a ba tana can gaban Tvn kowa ya shige d'aki ya barta. Asghar ma anan falon ya nemi guri ya zauna yana kallon Nusrat had'e da Nazarinta a hankula. Tun da baiga Hajjaju a falon ba yasan tana bedroom inta don haka ya nufeshi kai tsaye, sai da ya d'an tsaya yayi nocking kafin yaji muryarta tana fad'in. "Shigo Turaki." Baiyi mamakin sanin da tayi shi d'in bane saboda duk wanda yazauna tare da shi to tabbas zai haddace k'amshinsa bare ita tasan yadda nocking insa yake, banda shi kuma babu me tunkaro inda bedroom inta yake to sai yanzu da Nusrat ta shigo cikin rayuwarta." "Na sameki lafiya" "Lafiya lau, ya naka jikin?" "Alhmdlillah, ya guiwoyin naki?" "Yanzu ban jin ciwon komai, wannan yarinya da ka kawomun ina matuk'ar jin dad'in zama da ita, ita take mini tofi kuma ta shafe mini da man zafi." Bai ce komai ba,kuma tasan bazai ce d'in ba don haka taci gaba. "Baffanka k'arami ya kawomun k'ararka, sai yaushe ne Turaki za ka cika burin mahaifinka? ba ka samu kayi hakan yana raye ba, amman yanzun ya kamata ka k'ok'arta, ina son ganin rayuwarka ta dai daita kamar kowa, ka manta duk abinda ya faru a baya kasa gaba kawai a ranka, baya ta riga ta wuce baza ta tab'a dawowa ba don haka ka daina bata damar tab'a maka rayuwarka ta yanzu, ka manta komai kayi rayuwarka a sake ka daina k'untata zuciyarka, ina son ganin auranka, ina so na ganka tare da matarka kuna rayuwar farin ciki, ina so naga 'ya'yanka Turaki, ina so ina so da yawan Abubuwa su dai daita cikin rayuwarka tun kafin tawa rayuwar tazo k'arshe don bamu da tabbacinta." "Bazan iya ba Hajjaju zuciyata tana mun ciwo har yanzun na kasa mantawa, ina jin bazan tab'a mantawar ba, amman ki bar batun aure cikin rayuwata, k'addara ta riga ta saka almakashinta mai kaifi ta yanke aure daga cikin rayuwata." "Ba ta yanke ba Turaki, sai dai in kaine zaka yanke, ka gwada ka kuma bata dama." "Bazan iya ba Hajjaju bazan iya ba wallahi, zuciyata da k'wak'walwata ba zasu iya d'auka ba, bazan iya ba bazan iya ba nace." Ya fad'a jikinsa yana wani irin karkarwa yana kallon hannunsa yana ganin kamar yanzun ne yake d'auke da gawar Faleesha, ganin yadda ya birkice yasa Hajjaju jan bakinta tayi shiru, ta dawo tattofa mishi adda'a kafin tayi mishi cikin ruwa ta bashi yashi, had'e da rarrashin shi da gaya mishi kalamai masu dad'i. "Kici gaba da mini addu'a pls." Yakai k'arshen maganar yana jin kamar ya cire abinda ke k'irjinsa don yayi mishi nauyi, nauyi yadda baza ku fahimta ba. "Ban jin zan gaza da yi maka addu'a har zuwa ranar da numfashina zai tsaya, tashi muje muci abinci." Bai yi musu ba ya mik'e, don tabbas yana jin yunwar, bai sani ba ko rashin lafiyar da yayi ne yasa ya daina jin dad'in d'and'anon girkin Baba Azumi, kamar yadda a kwanaki yaji ya canja masa yana mishi matuk'ar dad'i, sai da ya fara sabawa da shi kuma ya canja masa zuwa d'and'anon da bai jin dad'insa a harshe ya fi sonsa gaskiya, amman haka yake daurewa yana turawa saboda yunwa gashi ba ma'abocin cin abincin waje ba. "A'a Asgharu tare kuke ashe." Cewar Hajjaju tana kallon Asghar cike da fara'a, murmushi shima yayi had'e da amsa mata da. "Wallahi kuwa Hajjaju tare muke, ya jikiin naki?" "Jiki Alhamdlill Asgharu gashi yauma zan hau dining abinda na kwana biyu ban yishi ba, ai zuwan wannan yarinya alkhairine cikin rayuwata, ya ka baro mini kishiyoyina?" Sai da ya fara sauke idonsa kan Nusrat in yana jin zuciyarsa na kuma nutsuwa da ita kafin ya bawa Hajjaju amsa daa. "Kai amman naji dad'i Allah ya k'ara lafiya, wallahi suna lafiya suna gaida ki." "Amin, ina amsawa, taso muyi dinner tare." Ta fad'a tana daidaita zamanta akan kujerar dining in, shikwa Aashiq tuni dama ya zauna yana amfani da wayar da ke hannunsa. A hankula ta taso ta fara serving in Hajjaju, kafin ta matsa gefen da yake tana serving insa shima tana amsar yadda zuciyarta ke wani irin dokawa, har ta gama serving insa ta yiwa Asghar ma kana ta yiwa kanta ta ja kujera ta zauna itama duk da tana jin kamar ba ta can canci hakan ba, kamar matsayinta bai kai nan ba,amman ba ta da k'arfin barin gurin saboda Hajjaju. Duk da k'amshin abincin da ke sirarowa yana shiga k'ofofin hancinsa, yana jin kamar irin k'amshin abincin da yake muradi amman bai ajiye wayar ba ya fara cin abincin sai da Hajjaju ta d'ago ta kalleshi had'e da fad'in. "Turaki ba za ka ja abincinnan kaci ba sai ya huce, kai da ba ka son hutaccen abinci." Gabanta ne yayi wani irin fad'uwa jin sunan da Hajjaju ta ambata,don wannan ne karonta na farko da taji sunan a bakin Hajjaju don tun zuwanta gidan bai zo ba sai yau d'in da ya d'ebi kusan sati biyu a kwance bashi da lafiya, ji tayi kamar yanzu ne mutumin nan na mafarkinta yake furta TURAKI, ga wani turakin gabanta sai dai ba ta da tabbacin shi d'inne ko ba shi ba ne. A hankula ya ja farantin ya fara ci, yana jin yadda d'and'anon ya zauna a harshensa kafin ya d'au cup in black tea yakai bakinsa, shima jinsa yayi yadda yake so yadda kuma yake muradi, ba mamaki wannan yarinyar zuwanta ita ta kamawa Baba Azumi girki shiyasa d'and'anonta ya zauna masa a harshe bayan barinta gidan kuma ya kasa dawo da d'and'anon Baba Azumi na daa da ke bakinsa, duk da itama Baba Azumin ba baya bace gurin iya girki sai dai wannan yafi zamar masa sosai. "Ka dawo kusa da ni da zama." Cewar Hajjaju tana kallonsa don jiran me zaice. "Dama ai kece kika koremu." "Na koresu dai, kai kuma ka bisu, ka janye mini Aleesha ma, ni kuma naji bazan iya hanaka ba, amman yanzu ina buk'atar ka dawo nan gaba d'aya." Gyad'a mata kai kawai yayi yana cigaba da cin abincinsa itama kuma ba ta k'ara komai akan hakan ba sai Nusrat ta kalla da ke ta jujjuya cokali cikin plate in." "Idan zaman anan yana takuraki, ki d'auka kije can d'aki kici." Kamar jiran umarnin hakan take tayi hanzarin mik'ewa tana barin gurin. "Tana da hankali, ga nutsuwa ga tsafta,uwa uba ga iya girki,a sashin nan bani da wasu masu girki tace a sallamesu komai ita take mini ba ta gajiya." "Na fuskanci hakan nima Hajjaju, don na matuk'ar jin dad'in girkin nan sosai." Cewar Asghar, shi kwa Aashiq bai ce ba kuma sun san bazai ce d'in ba. 。。。 "Zaki iya taimakona gurin ganin rayuwarsa ta dai daita?" Asghar yace da ita, bayan d'an sabon da ya shiga tsakaninsu na kwanaki, musamman da Aashiq ya dawo gidan da zama sai ya zamana kusan kullum da daddare zaizo suyi dinner tare kuma yakan jaa Nusrat in da 'yar hira haka har ta saki jiki da shi, ko babu komai yafi wancan da ko gaisuwarta ba ya amsawa ba ma ya nuna yasan da tsaiwarta a gurin da yake. Tasan akan wa Asghar in yake magana,sai dai ba tasan ta ina za ta iya taimakawar ba, bayan ba ta san matsalarshi ba, sai dai wanda ya zauna da shi ne kawai zai gane babu nishad'i a cikin rayuwarsa, ko murmushi zai yiwa Hajjaju idan ta kama, to yakan zo ne babu nishad'i ko kad'an a cikinsa a hak'ik'anin gaskiya yadda ta fahimta rayuwarsa a mugun k'untace take, za ta so itama ta taimaka d'in musamman da taji yanzun Asghar ya gaya mata sai da taimakon wine ko cocaine yake iya bacci, amman ba ta san ta yaya za ta iya taimakawar ba . "Ina so na taimaka d'in, amman kuma bansan ta ya ya ba." "A hankula nake so ki shiga cikin rayuwarsa ki zauna." "Idan na shiga cikin rayuwarsa na zauna, ni kuma tawa rayuwar fa?" "Ina ji a jikina rayuwarku za ta cure ta zama abu guda d'aya ne insha Allah." "Ta ya kake zaton hakan zai kasance, bayan ko kallo ban isa a gurinsa ba?" "Ke kike ganin hakan Nusrat, amman kin dad'e da zama cikin idanuwan Aashiq wannan dalilin ne yasa ba ya son kallonki saboda ba ya k'aunar alak'arki da su, saboda ya riga ya,haramtawa zuciyarsa motsi akan kowa, ina so ki k'aryata hakan,ki nuna masa bashi da ikon yin yadda yaso da rayuwarsa wannan ikon yana hannun mai duka ne, ina so ki kasance a duk inda zai kasance, kuma kiyi abinda zaki janyo don dole ya kalleki, ta silarki muke saka ran dawowar nishad'i cikin rayuwarsa , kada ki ruguza mana haka pls ina rok'anki" "Zan gwada" "Ni kuma zan taimaka, Allah ya bamu nasara amin" Turare ya bata wanda za ta dinga yi ta tabbatar Aashiq in ya shak'a, sai tofi da rubutu wanda yace ta dinga mishi amfani da su gurin black tea in da yake so, ta fara mishi amfani da rubutun da tofin amman turaran ne har yau ba ta samu damar hakan ba, kuma ba ta gano ta inda za ta shiga cikin rayuwarsa ba don yanzu sai taga kamar ma yafi d'aure mata fuska akan daa.... Game da masu bukatar haihuwa. 1-Hurmul,ki dafasa ki zauna a ciki, kiyi kamar sau uku a sati, zaa dace indai mijinki ya sadu dake, idan Allah ya kawo rabon. 2-D'anyar gyad'a,ki dakata sai kina sha da ruwan d'umi. 3-Man rid'i, kina shafashi a mararki. 4-Yayin da kuna saduwa kina karanta Astagfirillahil azim wa atubu ilaihi. 5- ki soya k'wan agwagwa da man tafarnuwa ki ci. Allah Ubangiji kasa mu dace. [6/8, 6:01 PM] Rabi: 39 ~BAYAN WATANNI UKU~ Har zuwa wannan lokacin Asghar bai daina kawo mata tofi da rubutu ba ita kuma sai ta dafa mishi shayi da shi saboda mayan black tea ne safe rana yamma dare sam ba ya gajiya, turaran kuma ta samu damar yi masa amfani ne ta hanyar gyara masa d'aki da take yi, kasancewar babu wasu masu aiki da suka rage a sashan kuma bazai yuhu kartin namiji ya dinga shigo musu ba don shine yake yi mishi a can gidan Baba Azumi kasancewar yana da k'ofarsa ta shi kad'ai nan kuwa dole sai ka ratso ta falon kana za ka hau matattakalar da za ta kaika zuwa sashensa. Yawanci duk sanda za ta yi gyaran yana nan bai fita ba,kasancewar ba office yake zuwa ba, sai dai in zashi ziyartar gidan marayu ko asibiti don ba da jini ko kuma gurin su Baba Azumi ko gun Baffanninsa kuma yawancin fitar tasa da yamma yake yi, in ta gyara falo ta kan k'wank'wasa mishi domin ya dawo falon ta gyara ciki, to sai ta tsaya rik'e da garwashin da ta wura ta kuma zuba turaran a ciki idan ya fito ta tabbata zai shak'a a haka ta dinga masa amfani har ya k'are. Ba za'ace ba'a ganin ci gaba ba,don sosai ya rage shaye shayen nasa ba kamar daa ba, tsakaninshi da Nusrat kuwa gaisuwa ce in yaga damar amsawa, duk wani kakkauce matan da yake bai hana ta k'ara yin kusancin da idanuwansa ba, tana motsa dukkan wani gurbi da yayi tunanin ya dad'e da daina aiki cikin zuciyarsa ba kuma zai kuma tashi ba, amman Nusrat tana k'ok'arin k'aryata tunaninsa don sosai yanzu zuciyarsa take doka mata,hakan yasa shi kuma d'aure mata fuska fiye da daa, don sam ba ya k'aunar kusancin da zuciya da idaniyanshi suke nema daga gareta, banda bakinsa da yasaba da d'and'anon abincinta da tsaf zai iya komawa can gurin su Baba Azumi to ya tabbata cin abinci zai kawoshi gidan, anyi ba'ayi ba kenan. Had'uwarsu ba ta wuce zama cin abinci a dining ba, wanda Hajjaju ce ta tilasta mata zaman, tun ba ta sake ba har tazo ta sake gaba d'aya,to sai idan taje mishi shara idan ya dawo falo za ta gyara bedroom in, ta rasa me yasa zuciyarta take buk'atar kusanci da tasa zuciyar har take doka mishi a duk sailin da ta ganshi ko taji muryarshi,ko giccinsa ko takunsa. A hankula ta jishi yana shiga cikin zuciyarsa yana samun guraben da Rj ya bari cikin zuciyarta,ko kad'an ba tayi tunanin Rj ya bar space cikin zuciyarta da har wani zai fara tunanin shiga ba sai da zuciyarta ta fara dokawa Aashiq,taji ya cika ko ina ko k'aramin guri bai bar mata ba bare gurin da za ta shak'i iska, ya cika ko ina taf da sanyayyar k'aunarsa wacce tayi mata kamu ba d'an kad'an ba domin ta kaita k'arshen tik'ewar tik'ewa. Ko da wai ba tayi tunanin littafin k'addararta zai bud'e mata wannan page in ba, page in fad'awa soyayyar wanda ko kallo ba ta isa a gurinsa ba, gaisuwa ma idan tayi masa sai yaga damar amsawa itama amsawar kamar an mishi dole,kullum tunaninta ta ina za ta fara duban wannan page da idon basirar da za ta fahimci abinda ke ciki ta samu damar cinye jarabawar cikin sauk'i,kafin a kuma bud'o mata wani sabon shafin. 。。 Yammacin yau zamu iya kiransa yammacin da sam taji ta gundura da shi ko kad'an ba ta jin dad'insa,jiya Yusra ce ta zo suka huni suna shan hirarsu cikin farin ciki, shiyasa yau in ta jita a takure,ga Hajjaju bacci ya kwasheta kuma ta gaji da danna wayarta da Hajjaju ta saka Aashiq in ya siyo mata ita,ji tayi tana son shak'ar iskar waje ba irin ta cikin falon ba don haka tayi fitowarta waje tana kallon korayen fulawoyin da aka k 'awata harabar cikin gidan da ita, jikin wata pulawer da take bada ruwa ta k'arasa tana sanya hannunta cikin ruwan, a hankali ta fara jin nishad'i har da sakin murmushin da ba tasan tana yi ba. Da k'afa ya fita saboda iyakacinsa gidan Baffa ne da na Baffa k'arami, sai gashi sun shigo da Aasad yana gaya mishi cocain in da yace a kawo mishi yau da daddare zaije ya anso ya kawo masa, duk da yayi mamakin baice har da giya ba, don yaci ace wacce ya kawo mishi ta k'are duba da yadda yake shanta amman baice komai ba ya bari sai ya kawo mishi cocaine in sayi maganar. Lumshe idanuwansa yayi ya kuma bud'esu akan Nusrat yana jin wani irin abu da yake fusgarsa zuwa gareta bai san sanda k'afafuwansa suka fara takawa suka nufi gurin da take a tsaye ba. Ganin inda Aasad in ya nufa yasa Aashiq d'ago kanssa don ganin gurin, saboda shi kanshi a k'asa yake. Doguwar riga ce a jikinta, wacce ta amshi kalar fatarta ta kuma zauna a jikinta, zai iya rantsuwa bai san tana da wannan sirrin kyahun ba sai yau d'innan,sabili kuwa da kullum cikin hijabi take duk kwa da fad'an da Hajjaju take mata kan saka hijabin ko da yaushe har ta hak'ura ta k'yaleta ganin ba ji za ta yi ba, yau d'inma bai san me yasha kanta ta fito a haka in ba, ji yayi zuciyarsa tayi zafi ransa ya b'aci musamman da yaga irin kallon da Aasad yake mata yana nufar gurin da take kamar wanda saitin kansa ya kunce sai lashe baki yake kamar wani tsohon maye, wata gigitacciyar tsawa ya doka mata had'e da fad'in ta b'ace masa daga gurin, a firgice ta d'ago don ita ba ta san da shigowarsu ba sabili da hankalinta ba ya gurin, cikin idon Aasad da ke gab da k'arasowa inda take idonta ya fara sauka, wanda yaji wani irin jiri da zazzab'i zazzab'i da ya kamashi lokaci guda saboda k'wayar idonta da ta sauka cikin tasa, kafin ta janye idonta ta mayar kanAashiq da ke wani irin huci da fushin da ba ta tab'a gani akan fuskarsa ba, da wani irin sassarfa ta juya ta bar gurin ko waigowa ba tayi ba tana jin Aasad yana fad'in "Ki tsaya don Allah" Ita kuma tunanin inda tasan fuskarsa da muryarsa ta tafi. "Me yasa ka koreta?" Yake tambayar Aashiq in da wani irin fushi akan fuskarsa, baice masa komai ba ya rufawa Nusrat baya,yayin da Aasad shima yabi bayanshi,yana k'ok'arin rufo k'ofa ya sauke masa rikitattun idanunsa had'e da fad'in. "Ko da wasa kada tunaninka yasa k'afarka ta tako cikin gidannan." Saurin rik'o hannunsa Aasad yayi had'e da fad'in. "Mutumina yaushe ka shigo garine babu labari? ai dole kayi kishi akan wannan luu luun zinaren da zaka bani aro da na d'and'ana duk da daa son aure nai mata don ta tsayan a zuciya." D'aya hannunsa yasa ya naushi bakinsa nan da nan kwa ya fashe kafin yace. "Yaushe banzan tunaninka zaisa kayi mini wannan kallon,da ace ina da dama da tuni na rabaka da wannan halayyar akuyoyin shine ni zan jefa kaina a ciki? Ban san har iya haka ka tsane ni ba Aasad,abu na k'arshe kada ka k'ara nunan fuskarka." Yana kawowa nan ya fisge hannunsa had'e da doka k'ofar ba ya tunanin ta sameshi a fuska, da baiyi saurin ja baya ba kuwa da tabbas za ta sameshi a fuska, juyawa yayi cike da b'acin ran Aashiq in duk da danneshi da yake yi saboda yana da buri akan Aashiq, alk'awari ne bazai barshi yaji dad'in rayuwa ba. "Kai kuma kai da wa?" Cewar Baffa k'arami yana kallon Aasad. "Ni da Aashiq ne" "Sau nawa zance ka dinga danne zuciyarka akan Aashiq domin fushi babu inda zai kaimu." "Da bana dannewa da bamu kawo yau ba, da kuma yau anyi hargitsin da ba'a tab'a yi a cikin estate innan ba, yace kar na kara nuna masa fuskata." Cike da salllalmi Baffan yake kallon Aasad in yana ganin zai rusa musu damarsu akan Aashiq in kafin Aasad in yaci gaba da cewa. "Kada ka damu Baffa, shi zai nemeni,zai nemeni da kansa a daren nan kuwa." Yana kawowa nan ya bar gurin mahaifin nasa,na binsa da ido. 。 Wani irin tiriri zuciyarsa take masa, sai juyi yake akan gadonsa ya kasa bacci ko kad'an, gashi bashi da wani abu da zai sakashi baccin, kuma bai jin zai nemi Aasad yadda zuciyarsa take tafarfasa akansa, sai dai yau tabbas yana jin zaiyi abinda bai tab'a yiba wato shan wani abun maye a waje, a hankali ya kunna hasken wayarsa da ya nuna masa karfe daya na dare, mik'ewa yayi tsaye yana zira jallabiya had'e da kiran wayar khalil. Farkawa tayi tana jin k'ishirwa kuma ta manta ba ta shigo da shi ba don haka ta fito falo don ta sha, bayan ta sha ne sai taji kamar har da yunwa don haka ta nufi kitchen kai tsaye. Inda ake ajiye muk'ulli ya duba bai gani ba, ganin haske a kitchen da kuma motsi yasa shi nufar can, tana tsaye tana goge hannunta, tun dosowarsa kitchen in tajiyo k'amshinsa da takunsa cikin k'irjinta, rintse idonta tayi tana jin yadda zuciyarta take doka masa kafin taji sautinsa. "Ke ina key?" Yi tayi kamar ba taji me yace ba,ta juya za ta bar kitcen in ya fisgota da hannu aya yana had'ata da bango... Game da wacce ta haihu ruwan nono yak'i zuwa. 1-Habbatus sauda a dafa a shafa a nonon 2-Hulba a dafata asaha kofi biyu kar a barshi ya huce 3-Na'a Na'a a dafata asha kofi biyu 4-Al-yansun idan kikayi sha[6/8, 6:01 PM] Rabi: 40 Sauke mata rikitattun idanuwansa yayi yana jin b'acin ransa yana dad'uwa, take mata k'afa yayi had'e da fad'in. "Ko da wasa kada k'afarki ta kuma taka harabar gidannan, in ba haka sai na kakkarya su, kuma in aka danna k'ararrawa ki tabbatar kin lek'a kinga waye, idan kika ga fuskar wancan mutumin ko wanda ba ki sani ba kada ki sake ki bud'e." D'aga mishi kai tayi,idanuwanta suna cikowa da hawaye don taji zafin take mata k'afar da yayi. "Ki bud'e baki ki amsa mini." D'ago da idanuwanta tayi ta saukesu cikin nasa, saurin janye nasa idon yayi don bai cika son mutum yana kallon cikin idonsa ba, ba ma ya bari hakan ta faru itama shammatarsa tayi har sai da ta motsa zuciyarsa. "Toh" Tace da muryarta kamar za ta fashe da kuka. "Ki bani key." "Kafata" Ta fad'a don ta kasa jurewa har lokacin bai d'aga mata k'afar ba kuma sai rad'ad'i take mata, d'auke k'afar tasa yayi daga kan tata yana sauke idonsa a kai yaga yadda tayi jaa sosai, ji yayi zuciyarsa tana umartarsa da yace mata sorry amman yaji sam bazai iya ba. Saka mishi key in tayi a hannunsa had'e da fad'in. "Zab'i ya rage naka walau kaje kasha abinda zai fitar da kai daga hankalinka kayi bacci cikin fushin Ubangiji walau kaje kayi sallah ko ka d'au Qur'ani kayi bacci malaiku na gadinka cikin rahamar Ubangiji." Tana kawowa nan tayi saurin barin kicin in duk da d'ingisa k'afar da take yi don sosai take mata zafi, a d'an corido in da zai sada ka da bedroom insu ta tsaya tana jiran ganin abinda ya zab'awa kansa. Mutuwar tsaye yayi yana bin gurin da ta b'ace da kallo, ko da wasa bai tab'a tunanin ta san yana shan wani abun maye ba saboda taka tsan tsan in da yake sam ba ya son mutuncinsa ya zube a idon wani, banda Asghar da Aasad zai iya rantsuwa babu wanda ya san yana shan abin gusar da hankali sai kwa Khalil shima dalili don shine amintaccansa duk cikin yaransa, duk wani tunani yayi ya kasa sanin ta inda Nusrat ta san yana shan kayan maye don ko kad'an bai bata k'ofar sanin hakan ba. Jiki a sanyaye ya fito daga kicin in, bayan ya ajiye key in kan teburin cin abincin da ke kicin in, ganin ya fara taka matattakalar benensa yasa Nusrat sakin ajiyar zuciya me nauyi me kuma k'aramin sauti kafin ta juya ta nufi bedroom insu itama, ji yayi kamar wanda aka tasa daga bacci, kamar wanda akewa kira yabar abinda yake aikatawa ya koma wani, ji yadda yake jin ya muzanta saboda 'yar k 'aramar yarinyarnan tasan abinda yake aikatawa, ina ga mahaliccinsa, shin ya manta yana kallonsa a duk sanda ya d'aga kwalbar giya ko ya shak'i cocaine, ya manta da in ya b'oyewa mutane bai isa ya b'oyewa mahaliccinsa ba, kaico kaico ina tunani da hankalinsa ya tafi ya manta da duk wa'yannan, bazai iya tuna da yaushe ne ma hannunsa ya fara tab'a kwalbar giya ba, inama inama inama baya za ta dawo da ya gyara kuskuran da yayi a baya, da bai gurb'ata rayuwarsa da shan kayan maye ba, da bai bari tunaninsa ya kunce masa ba har ya manta da Qur'ani shine maganin damuwa ba abin gusar da mayen da zai cutar da kai wata rana. A wannan dare ganawa yayi da Ubangijinsa sosai yana istigfari da neman dai daito cikin rayuwarsa kafin ya d'auki Qur'ani ya fara karantawa bai san sailin da bacci yayi gaba da shi ba har ya kusan makara a sallar asuba, sai dai ya tashi da matsanancin ciwon kai wanda ko masallaci bai barshi yaje ba sai anan yayi sallar a daddafe kana ya koma gado ya kwanta don zazzpab'i ya fara rufeshi. Bayan sunyi sallar asuba komawa tayi baccinta saboda ba da wuri suke karyawa ba shiyasa take komawa bacci sai k'arfe takwas ta tashi ta hau aiki,yanzunma k'arfe takwas in ta tashi, zuwa sha d'aya da rabi ta kammala komai har wanka tayi kana suka zauna a dining yin break fast, har suka kammala Aashiq bai sakko ba, da wuya kuma har su kammala bai sakko d'in ba wani zubin ma yakan rigasu zama akan dining in, kallon Nusrat Hajjaju tayi had'e da fad'in ‘’Ki shirya mishi nasa ki kai masa, ina jin dai ba lafiya ba.‘’ "Tom"Tace kafin ta d'auko babban tray ta had'a masa break fast in nasa a kai, had'e da tea in da ta dafa masa da garin maganin da Asghar ya kawo mata jiya, ta tace shi tsaf ba za kace da garin magani aka dafasa ba, kafin ta d'auki tray in ta haura sama, akan dining ta ajiye kana ta fara gyara falon duk da ba wani datti yayi ba kafin ta k'arasa jikin k'ofar bedroom in nasa ta fara knocking, gajiya tayi da tsaiwa don ko alamun motsi ba ta jiyo ba bare kuma gyaran muryar da yakan yi mata wani zubin in yana toilet, d'an bud'e k'ofar tayi a hankula tana huhhurga idanuwanta ta inda za ta ganshi ba taga komai ba don haka ta k'arasa bud'e k'ofar ta shigo a hankula sai da ta kawo tsakiyar d'akin kana ta hangoshi a tsakiyar luntsumeman gadonsa ya rufa da bargo gaba d'ayansa juyawa tayi da niyar barin d'akin kafin taji muryarsa cikin yanayi na ciwo yace. "Taimaka ki had'an ruwan wanka." Juyowa tayi har lokacin yana rufe bai bud'e fuskarsa ba, kamar ta tambayeshi bashi da lafiya sai dai ta ja bakinta tayi shiru ta nufi toilet in nasa. Sai da ta had'a ruwan ta bar d'akin kana ya yaye bargon ya fito sai had'a zufa yake da alama zaxzapb'in ne ya sauka, wanka yayi ya yo brush kana ya fito, sai da ya goge ruwan jikinsa kafin ya shafa mai da turarukansa masu k'amshi da matuk'ar tsada, kana ya fito don a gaggauce yake komai cikinsa ya fara kiran ciroma idan ba gizo irin na hancinsa ba har k'amshin girkin Nusrat in yake jiyowa daga d'akin, baiyi tunanin samunta a falon ba amman yana bud'e k'ofar cikin idonta idanuwansa suka samu masauki zuciyarsa ta matse guri d'aya, ganin tray da yayi akan dining yasa shi nufar can, ashe dai hancinsa ba k'arya ya jiyo masa ba, a hankula ta mik'e ta bi bayansa, tana gama serving insa ya kalleta yace. "Thanks" Ko kad'an ba tayi zato ba ba tayi tsammanin jin wannn kalmar daga bakinsa ba, murmusshi ne ya kubcewa fuskarta don haka tayi saurin juyawa don kar ya gani sai dai kaish ta makaro don ya riga ya gani har yayi sanadiyar saukar da murmushin a tasa kyakkyawar fuskar yana bin bayanta da kallo cikin wani yanayi mara misaltuwa wanda umarni daga zuciyarshi ba daga gareshi ba. Bedroom insa ta nufa tana jin yadda zuciyarta take matsewa guri guda, akan sofa ta zauna sai da ta dai daita nutsuwarta kafin ta tashi ta hau gyaran d'akin, shi kuwa bayan ya gama break in falo ya dawo ya zauna yana danna wayarsa kafin yaji cikinsa ya fara wani irin yamutsawa da murd'awa can yaji wani abu ya fara taso masa kamar amai da hanzari ya nufi bedroom in nasa, ta gama gyaran d'akin kenan za ta fito ya banko d'akin ya shigo d'akin a gigice toilet ya nufa a bakin toilet in ya zube ya fara kelaya wani bak'ik'k'irin in amai cikin muguwar azaba, tun yana yi da k'arfinsa a kuzarinsa ya k'are cikin fitar hayyaci yake cewa. "Me kika bani naci,me nayi miki,wa ya turo ki,me yasa kika zab'i kasheni ta wannan hanyar?" Wani mugun tashin hankali ne ya ziyarci Nusrat ta fara girgiza mishi kai kafin hawaye ya fara wanke mata fuska cikin wata gigitacciyar tsawa ya kuma fad'in. "Ki gaya mini wa ya turoki ki kasheni?" Wani irin rawa jikinta ya fara yi kamar mazari ta fara karkarwa Cikin sauk'i idan kikayi yaye. 1-Ki sami hulba ki shafa akan nonon 2-Al suzab,al kazbara,gishiri,ki hadasu guri d'aya kina sawa a abinci kina ci,zai d'auke insha Allah. [6/8, 6:01 PM] Rabi: 41 Asghar ne ya bud'e k'ofar ya shigo, ganinsa da Nusrat tayi yasata sakin ajiyar zuciya amman hawayen bai bar zuba akan fuskarta ba. Mantawa yayi bai kawo mata rubutun da za ta bashi ba, bayan yasha shayin, tunawar da yayi ne yasa shi tahowa ya kawo mata, da yayi knocking Hajjaju ce ta taso da kanta ta bud'e masa, bayan sun gaisa tace da shi ya hau saman ya gano mata lafiya, tun d'azu ta tura Nusrat to itama ta jita shiru, tsawar da Aashiq yayiwa Nusrat ce tasa yasan suna cikin bedroom in dalilin da yasa kenan ya nufo bedroom in kai tsaye. Bata rubutun yayi kana ya nufi gurin Aashiq in da ya jingina da k'ofar toilet in yana mayar da numfashi, taimaka masa yayi ya gyara jikinsa, kana ya kamosa ya kwantar da shi akan gado ya koma ya gyara toilet in, bayan yacewa Nusrat ta juyo rubutun a cup ta kawo, da k'yar ya karb'i rubutun yasha da yak'i sha yace k'arasa shi zasui, sai da Asghar in ya lallab'a shi ya nuna masa in yasha shine zai samu sauk'in ciwon da yake ji, yana shan rubutun ba jimawa bacci yayi awan gaba da shi. Kallon Nusrat Asghar yayi yace. "Kiyi hak'uri, zafin ciwo ne ya saka shi yi miki wannan tambayar, kije k'asa ki sanarwa Hajjaju zazzab'i yake fama da shi, yasha magani ya samu bacci, ni zan zauna da shi." Gyad'a mishi kai tayi kana ta fice daga d'akin. 。。。 Kwanansa hud'u yana fama da ciwo, Asghar da Nusrat ne masu jinya duk ya shagwaggwab'esu don akwai shi da raki indai yana ciwo sai dai in babu wani kusa da shi, don Asghar cewa Ramla yayi ta tafi gida shi kuma ya zauna yake kwana da shi, don Nusrat ba za ta iya da shi ba,ko da kwa ace matarsa ce, a kwana na biyar inne ya tashi ras da shi kamar bai ciwo ba sai dai 'yar ramar da yayi fuskarsa tayi fayau. Daga wanka ya fito ya shirya cikin k'ananan kaya na shan iska, Asghar tun jiya da daddare da yaga jikin nasa yayi d'an dama yaje ya d'auki matarsa suka huce gida, falo ya fito ya zauna yana sauke idonsa kan agogo yaga har sha biyu saura, ko me Nusrat take har yanzu ba ta kawo mishi break ba? "Mtsssss" Yaja tsaki had'e da dak'una fuska sai kuma yaji k'arar bud'e k'ofa ya zubawa k'ofar ido, da sallama ta shigo a bakinta duk da tasan bai zama lallai ta sameshi a falon ba, ganinsa zaune a falon yasa ta d'an dakata tana zubawa fuskarsa ido kamar yadda ya zubawa tata idanuwan, don a rashin lafiyar nan da yayi ya riga ya sallamawa idanuwansa yabi umarnin da yake bashi. "Barka da safiya,ya k'arfin jiki?" Me makwan ya bata amsa sai ya shagwab'e mata fuska yace. "Da alama yau so kike ki k'arasani shiyasa kika hanani abinci, gashi yanzu ma kin taho hannunki haka." "Naga jikin naka yayi sauk'i ai, shiyasa nayi zaton za ka sauko, da yake Hajjaju ma tana son ganinka." "Ai sai na gaya mata kin kusa kashe mata jikanta." "Daga taimako, kuma nima bani akai na saka maka,da ace nasan zai wahalar da kai haka da ban saka ba" Tasowa yayi yana nufo inda take a tsaye yayi k'asa da muryarsa had'e da fad'in "Saboda kin damu da ni?" Ba za ta iya cewa eh ba ko a'a don haka tayi saurin bud'e k'ofar ta fice,had'e da fad'in "Ka fito yanzu su Baffa suna jiranka" Da d'an k'arfi yadda zai jiyo, bin bayanta yayi da murmushin da ya fito daga can k'asan zuciyarsa wanda rabon da yayi irinsa tun akan Faleesha, d'an dukan kansa yayi had'e da tambayar. "Me ke damunka neAashiq?" Kafin yasa kai ya fice. (To nima dai bani da wannan amsar,sai dai kuci gaba da biyo alk'alamina zai baku amsa.) 。。。 A yanzu Aashiq ko kwalbar giya ya tsani gani bare kuma cocaine, da na sani yake a baya ma da ya shata, yana tunanin inda k'arfin imaninsa ya tafi a lokacin da k'addara ta bud'o masa shafin jarabawar da ya kasa karb'arta. Ba zaice yanzu ba ya jin dad'in rayuwar ba, don k'unci da damuwar nan duk yanzu ba ya jinsu, yana baccinsa a ko da yaushe idan ya so ba tare da yasha abin gusar da hankali ba, lallai Asghar da Nusrat haske ne cikin rayuwarsa don har yanzu ba su barshi haka ba sun mayar da rubutu ruwan shansa kuma yana jin dad'i sosai k'wak'walwarsa da zuciyarsa fresh yake jinsu. Damuwarsa d'aya ce yanzu idan ciwon mararsa ya motsa yakan ji kamar zai mutu sai ya raba dare kafin bacci ya d'aukesa, maganin yanzu ya daina d'aukarsa sai allura ita kuma likita ya sanar da shi za ta bashi matsala, yana d'aya daga dalilin da ya k'ara k'arfin shan giyarsa yana sha in ya make shikenan yanzu kuwa da ya daina shan giyar sosai ciwon ya matsa masa, bai san ya zaiyi ba abu d'aya ne idan ya jewa likitan kayi AURE, kalmar da ya tsani ji a duk fad'in duniyar nan idan har a kansa ne, domin alk'alamin k'addara ya dad'e da musu zanen Katanga tsakaninsa da AURE. Ba kuma zai iya zina ba, yafi kowa k'yank'yaminta don tun a tashan k'uruciyarsa Aasad yake ta jan ra'ayinsa amman yak'i duk kuwa da kasancewarsa mabuk'aci sai ya gwammace gara yayi aure ko da babu soyayya amman ina auran sai ya gagara domin k'addara ta riga ta gifta a tsakaninsu, amman duk da haka ya kau da idonsa daga mata ya toshs kunnansa da duk abinda Aasad zaice masa. Hankalin Aasad idan yayi dubu ya tashi, musamman yanzu da yaga Aashiq da Asghar sun had'e sun kuma k'ullewa, amman shi ko wayar Aashiq in ya kira ba ya d'agawa, bai tab'a tunanin a ranar da suka samu sab 'ani zai iya bacci ba tare da ya neme shi ba sai gashi har aka shafe way'annan kwanaki ba tare da ya neme shi ba, idan yaje gidan haka zai tayi knocking ba za'a bud'e ba, Baffa K'arami ya had'asu yayi musu fad'a kan bai dace suna fad'a a tsakaninsu ba, amman duk da hakan bai sakar masa ba, ko da sun had'u duk zancen da zai masa daga um ne ko a'a, idan yayi mishi zancen giya ko cocaine kuwa yakan nuna mishi ba ya buk'atarsu yanzu, hatta su Baffa sun shiga d'imuwa da jin Aashiq ba ya shan komai a yanzu sun fara tunanin waye suke sara yake musu sassak'ainda kai tsaye Aasad yace Asghar ne, yayin da Baffan Asghar in yace zaiyi maganinsa kuwa, shine ya turashi Abuja yace ya koma can da zama ya dinga kula da harkokinsu na can gaba d'aya yafi sintirin da ake ana dawowa,baiyi musu ba ya d'auki matarsa da 'ya'yansa suka koma can da zama bayan ya kawo malamin da yakewa Aashiq rubutu gurin Aashiq in, aka bashi masauki a can bayan gidan, yacewa Nusrat a gurinsa za ta dinga karb'o rubutun Aashiq d'in in ya k'are. Tun da yayi sallar isha ya samu ya hau gado a daddafe don mararsa ciwo take masa dalilin da yasa bai samu yaje masallaci ba kenan, juyi uake akan gadon cikin matuk'ar azaba, shi kad'ai yasan azabar da yake sha, sai kuma Allahn da ya d'ora masa, tasbihi kawai yake yana kiran sunan Allah. Bayan sun kammala dinner Hajjaju ta kalli Nusrat tace "Ki kaiwa Turaki nasa, sai kizo kema ki kwanta, ni na shiga daga ciki." "Toh" Tace mata, bayan barin Hajjaju gurin, na Mallam ta fara had'awa ta tafi kai masa,duk da akwai masu yiwa ma'aikatan gidan abinci suna kaiwa ko ina amman malam ita take kai pmasa safe rana dare,kumama dai ba kowa ne yasan da zaman Mallam in a cikin gidan ba,ta k'ofar kicin da zata sadaka da bayan gidan take bi ta kai masa,banda ba'a mutuwa a dawo da babu abinda zai hana tace Mallam d'innan Babanta ne, suna kama sosai da Baba sai dai shi Mallam ya tara k'asimba da gashi sab'anin Baba da bai barin suma yakance ciwon kai take saka shi, tana jin kusanci sosai da shi, tana jin kamar ta sanshi kamar sunyi rayuwa tare,musamman yadda yake mata in taje gurinsa ya d'auketa tamkar 'yarsa ta cikinsa, itama kuma yana bata nata rubutun tana sha, yace rayuwa cikin mutane da ba ganin zuciyoyinsu kake a kanka ba sai da neman tsari. Bayan ta kaiwa Baba nasa tazo ta d'auki na Aashiq ta haura samansa, akan dining ta ajiye har za ta juyo taji kawai tana buk'atar sanin lafiyarsa, knocking tayi har kusan sau uku taji shiru, don haka ta murd'a k'ofar a hankula tana zira kanta ciki. "Zo ki bani ruwa" Yace haka don ya san ita kad'aice za ta shigo masa,kuma tunda suka ga bai sauka dinner ba yasan za'ta kawo masa. "Hajjaju ce tace na kawo maka dinner." "Ke dama ai komai Hajjaju ce tace,kizo ki bani ruwa nace." Yap fad'a har lokacin bai d'ago daga kwancen da yake ba,d'an k'aramin pridge in dake bedroom in ta k'arasa ta d'auko ruwan ta tsiyayo a cup ta kawo masa, a lokacin ya tashi ya jingina da fuskar gadon don haka ta zaga ta gefen da yake, mik'a masa tayi ya had'a da hannunta gaba d'aya ya rik'e yana sauke mata idanuwansa da suka k'ara girma suka lumshe saboda ciwon da yake cinsa,wani electrification suka ji a jikinsu, kafin su lumshe idanuwansu a tare su kuma bud'esu a kusan tare, cikin muryarsa da tayi wani irin k'asa yace. "Da tace ki kawon dinner tace kizo ki duba lafiyata?" Wata mitsiyaciyar kunya ce ta kama ta gashi dama a takure take da hannunta da ya rik'e, ga sanyin ruwan yana ratsa tafinta yana kuma saukar mata da wani irin yanayi, k'asa tayi da kanta ta fara k'ok'arin k'wace hannunta ganin hakan da yayi yasa ya rik'e cup in da d'aya hannunsa kana ya fisgota gaba d'aya ta fad'o jikinsa tana zazzare idanu cike da tsoro... Ciwon nono 1-Na'a na'a a dafata ta dinga gasa nonon sau uku a rana 2-Hulba a kwabata da ruwan zafi a shafa a nonon tun yamma har zuwa wayewar gari 3-Bak'in hims a dafa a ruwa a gasa nonon da shi, insha Allah zai sauk'i [6/9, 8:50 PM] Rabi: 42 K'ok'arin tashi take daga jikin nasa amman bai bata damar hakan ko kad'an ba, sabili kuwa da ba rik'o yayi mata na wasa ba, sai da ya shanye ruwan da ke d'aya hannunsa ya ajiye cup in akan bedside drower kana ya birkita da ita ta haye kan gadon sosai kafin ya rank'wafa kanta yana sauke idanuwansa akan fuskarta, sosai tsoro ya bayyana akan fuskarta,idan ta d'ago za ta mik'e sai ya mayar da ita nan da nan idonta ya kawo ruwa, me ke shirin faruwa da ita,wani shafin kuma k'addara take shirin bud'e mata, ba za ta so k'addara ta bud'e mata wannan shafin ba,shafin da ta san zai risketa da ta rok'i Allah ya d'au ranta tun kan ya nuna mata zuwan wannan rana. Rawa jikinta ya fara yi sosai yayin da Aashiq ya girgizata kafin ya rungumeta tsam a jikinsa, hawayen takaici da bak'in ciki ne suka zirarowa fuskarta kafin taji muryarsa yace. "Babu abinda zan miki, na kasa bacci ne so nake ki taimaka mini na samu bacci." "Amman kasan hakan babu kyau, tunda ni ba matarka ba ce?" "Na sani." "To don Allah ka cikani na tafi." "Bazan iya ba" Ya fad'a da wata irin murya yana k'ara rungumeta sosai, wani irin rauni yake jin zuciyarsa tayi, yana jin kamar ya fashe da kuka. "Don Allah ki taimakeni Nusss, idan kika tafi mutuwa zanyi, babu abinda zan miki wallahi asali ma ba halina bane, only sleep pls" Yakai k'arshen maganar yana kuma shigar da ita cikin jikinsa sosai, donma hijabin jikinta duk ya takura masa, sai dai bazai iya cire mata shi ba domin zai k'ara haifar da rashin yadda tsakaninsu. "Amman kasan da cewa ba zina bace kawai laifi, kusantarta ma babban laifi ne?" Shiru taji yayi bai bata amsa ba, don haka ta yunk'ura za ta tashi, taji babu hanyar da za ta iya mik'ewa ya riga ya sakar mata nauyi kuma duk yabi ya cukuikuyeta, da alamu bacci ya samu, baccin ma kuwa me k'arfi ne ya fugeshi da alamu ya tara shi da yawa, ita kuwa sam kasa baccin tayi don tsoro bazai barta tayi ba, Astagfirillah take ta ambata a ranta tana ganin duk laifinta ne, da ba ta shigo ba da hakan ba ta faru ba, amman an gama ta rufe shigowa sashensa idan har yana ciki, don ba ta san gaba me za ta haifar ba tunda aka fara da haka, baza ta ce ga lokacin da sarkin iya sata ya saceta ba, sai k'arar kiran sallar Asuba ne ya farkar da su a tare, fitilar gefen gadon ya zira hannu ya kunna kafin ya tashi a hankula ya nufi toilet yana furta kalmar "Thanks" Wanka ya soma yi, don wankan janaba ya hau kansa, ya riga yayi mafarki da Nusrat, abinda bai tab'a yi ba tun tashinsa sai yau d'in, jinsa yayi sakayau duk da a mafarki ne amman yana jin abinda ke mararsa ya ragu, don sharkaf ya jik'e wandonsa na ciki. Yana shiga toilet in ta yunk'ura da sauri ta fice daga d'akin, kanta tsaye ta bud'e d'akin nasu ta shiga don ta yanke ko da Hajjajun ta farka ba ta ganta ba za tace ruwa taje sha, sai kuma ta samu ma Hajjajun bacci take, don haka kawai ta nufi toilet, don wanka take buk'ata don gaba d'ayanta k'anshin Aashiq take ba iya kayan jikinta ba. Sai da ta fito daga wankan ta d'auro alwala kana ta tashi Hajjajun,lokacin har an kusa idar da sallah ma. Da matsanancin ciwon kai ta tashi,don haka Hajjaju ta hanata yin komai, ta k'wallowa Aashiq kira. "Kai Turaki,ka sauko aiki yau ya sameka Nusra babu lafiya kai zaka had'a mana break." Yana juyota don tunda yayi sallah bai kpma ba, yanzunma yana zaune a falo yana jin labarai, murmushi yayi ya tashi ya sauko, bayan sun gaisa ya nufi kicin in, Hajjaju na fad'in. "Sai a ramawa kura aniyarta, kaima kazo kai jinya,don Nusra da Asaghar sunyi matuk'ar k'ok'ari a kanka da baka da lafiya." Tea kawai ya dafa, sai k'wai da ya soya musu, Hajjaju za ta kira Nusrat in, yace bari ya kai mata d'aki, duk da shi bai yadda ciwon kan take ba. Tana k'udun dune cikin bargo, har ya shigo ya ajiye tray in hannunsa ba ta motsa ba. "Da alamu baccin bai isheki ba, bari nazo mu kwanta don nima tunda nayi sallah ban koma ba." Da hanzari ta yaye bargon ta diro daga kan gadon tana rarraba ido, dariya ya kwashe da ita sosai, zuba mishi idanuwa tayi, tana ganin yadda yake dariyar tun daga k'asan zuciyarsa ta fito, ba ta tab'a ganinsa yana dariya haka ba, dariyar tayi mstuk'ar k'ara masa kyau, ganin irin kallon da take masa yasa ya tsaya da dariyar shima ya zuba mata nasa idanuwan, sunaiwa juna kallon cikin ido, ko wanne yana d'iban sak'on dake ciki yana kuma bashi mazauni cikin zuciyarsa. 。。。。 Dukkaninsu ba zasu ce ga lokacin da wata k'arfarfar shak'uwa da soyayya ta shiga tsakaninsu ba, soyayya suke irin ta turawa, sun saba da rungumar juna kiss duk ba komai ne a gurinsu, sai dai idan aka cire kiss da huggin in ba su k'ara komai akan hakan ba, sai kuma bacci da suke cikin juna, tun Nusrat ba ta saki jiki da hakan ba, har tausayi da soyayyarsa ta saka ta saduda. Sun san ba dai dai suke aikatawa ba,kuma suna gudun wata rana shaid'an yafi k'arfinsu sai dai duk da hakan sun kasa dainawa, a duk lokacin da sukai yunk'urin dainawar sai su gaza inda Nusrat ta naima musu mafita d'aya kawai suyi aure, sam Aashiq ya nuna hakan ba mai yuyuwa ba ne, inda suka gabza gagarumin fad'a, fad'an da ko yini ba'ayi ba zuciyoyinsu suka gaza suka neme juna. Tabbas yasan ta fishi gaskiya a ko ina,ya za'ai su dinga abubuwa irin na ma'aurata bayan ba auranta zaiyi ba, shak'uwarsu k'ara k'arfi take tana gudun da ba su san bigiren da zata ajiyesu ba, yana jinta acan k'asan zuciyarsa itace farin cikinsa,rayuwarsa,ita ta fara gino Katangar farin cikin da ya dad'e da rusheta a babin rayuwarsa,bai tab'a nuna rauninsa ga kowa ba sai a kanta,zai shiga jikinta yayi kuka ta rarrasheshi ta sanya mishi nutsuwa a zuciyarsa, to ta yaya zaiyi sakacin da zata bar rayuwarsa?domin auranta yana nufin barinta cikin rayuwarsa har abada, anan kwa sai dai ya zamo mara adalci,don idan adalci zai mata ya fita daga cikin rayuwarta ya barta ta auri wani, sai dai yasan zuciyoyinsu duka ba zasu iya ba, don shi akan ya barta ta auri wani sai dai inkwa bazai zamo me adalci ba. Hajjaju kanta ta san da soyayya tsakanin Nusrat da Aashiq, sai dai ko kad'an ba ta san da rayuwar turan da suke ba, don ba sa yi a gabanta, ko kwanan da suke tare ba ta sani ba, da yake tana da nauyin bacci, idan tayi bacci Nusrat in take salallab'awa ta tafi,ana kiran sallar asuba sai ta dawo, ko da ta farka ba ta ganta ba, sai tace ruwa taje sha ko toilet ta shiga, sosai Hajjaju taji dad'in soyayyar tasu saboda ganin yadda tarayyarsu ta fara dai daita rayuwar Aashiq in, don yanzu da ka ganshi kasan yana tare da nishad'i, yaje ya samu Baffa akan ya shirya karb'ar aikinsa, inda hankalinsu yayi mugun tashi,sai dai ba su nuna masa ba sai murna da farin ciki da sukayi da hakan, musamman ma da suka san ba wani abu zai iya tab'ukawa ba tunda ba wani cikakken ilimi yayi ba. Yana karb'ar aikin ya fara sauya komai,duk wani abu da bai mishi ba ya fara gtara sa, ma'aikatan da ba su dace ba ya koresu,ya dakatar da na dakatarwa, don dakatarwar har kan Aasad ta biyo, bashi da wani aiki sai kwasar kud'in company yana abinda yaga dama, su kansu su Baffa matsayin iyayansa ya duba ya barsu akan kujerarsu don ba su cancanta ba, da fara aikinsa komai ya fara dai daita, abubuwa suka fara bunk'asa, ma'aikata sai murna suke da farin ciki, an fara biyansu yadda ya kamata, dama na can Abuja Asghar ya tsaya a kansa tsayin daka. Zuciyoyin su Baffa da Aasad ba'a magana don Aashiq ya sauya tunaninsu yayi abinda ba su tab'a tunani ba, don ba su san lokacin da ya k'ware a aiki har haka ba, sun fara tunanin abinda ya dai daita rayuwarsa don ta nan zasu bi su ruguza shi gaba d'aya, duk da Aasad ya gaya musu akwai wata yarinya da ya ajiye yana tunanin karuwarsa ce yana tunanin ita ta daidaita komai, sun dai ce zasu bincika koma mene ne dai zasu lalubo. 。。。 Kallonsa tayi da raunannun idanuwanta had'e da fad'in. "Ta ya'ya rayuwa za ta tafiyar mana a haka?Mu fa ba waliyai ba ne a ko da yaushe shaid'an yana tare da mu, kuma mun riga da mun san ba dai dai muke aikatawa ba, ina gudun kada shaidan yasa mu aikata abinda zamu zo mui da na saninsa daga baya, musamman ma ni, nice rayuwata za ta ruguje ta lalace,ko da ace kai ka aureni akwai ranar da bazan wuce gori a gurinka ba,don haka ka nema mana mafita, na gaji da wannan rayuwar da muke aikatawa" Takai k'arshen maganar tana fashewa da matsanancin kuka, dafe kansa yayi da yake jin kamar zai bar gangar jikinsa saboda tsabar ciwon da yake masa, ga kukanta da yake kuma har gitsa sa gashi tak'i yadda ya tab'ata,cikin raunanniyar murya yace. " Ni kaina ina tsoron wannan ranar ta riskemu,tunda ba mu muka halicci kanmu ba,har cikin zucuyata ba na son abinda muke,amman me na kasa dainawa,bani da wani buri da ya wuce na jiki cikin jikina a duk sanda idanuwana suka sauka akanki,ina so na daina amman na kasa,ki gaya mini ta ya zan iya dainawa?" "Ba za ka iya dainawa ba mafita d'aya ce kawai muyi aure" Ji yayi kansa yana mugun juyawa saboda kalmarta ta k'arshe da ta sauka cikin kunnuwansa, Aure aure ya shiga nanatawa a zuciyarsa kafin ya furta kalmar."No" Da d'an k'arfi,yana girgiza kansa. "Bazan iya ba,bazan iya ba,bazan tab'a bari k'addarar da ta samesu kema ta sameki ba,bazan iya,jure rashinki ba,domin rashinki na nufin rasani har abada." Kama kafad'unta yayi yana sanya tsumamman idanuwansa cikin nata yace. "Ina sonki Nusra,bazan iya jure rashinki ba zuciyata ba za ta iya ba,ke d'in jinin jikina ce tsokar jikina,bazan tab'a iya kwatanta rayuwa babu ke ba,don haka kibar batun aure tsakaninmu,k'addara ta dad'e da yimin ginin Katanga tsakanina da aure,kalmar aure ma bana son jinta Nusra don dole nake furtata da bakina a yanzu." Zare hannuwansa tayi daga kafad'unsa tana ja baya tace. "Zan bar duniyarka a yau d'innan,ka manta da wace Nusrat,ka cireni daga cikin tunaninka,domin baza ka sake ganin ko me kama da ni ba." Tana kawowa nan ta juya ta fice daga d'akin da gudu tana cigaba da kukanta, domin rayuwa babu Aashiq cikin rayuwarta masiface a gareta sai dai ya zamar mata wajibi ta jure dukkan wani yanayi da zata shiga muddun tana son tsira da mutumcinta, da kuma samun yafiyar Ubangijj kan kuskuran da sukayi a baya, tana jin lokacin komawarta gida yayi. Tana fita, shima ya fice daga gidan gaba d'aya, iska yake buk'atar shak'a ba irin ta cikin gidan ba,yana jin lokaci yayi da zai bar rayuwarta haka, tunda ta zab'i rabuwa da shi gara ya barta ta tafi d'in,don muddun yana d'ora idonsa a kanta bazai daina kusanta kansa gareta ba, gara tayi nesa da shi d'in tunda ko yaya ne in ya tuna tana shak'ar iskar da yake shak'a zai samu sauk'in wani abun. Kuka take sosai tana had'a kayanta a akwati, kallonta Hajjaju tayi tace. "Tafiyarki ba mafita bace a gareku Nusra, nasan akan maganar auranku kuka samu sab'ani ko?" Gyad'a mata kai tayi,tana share hawayenta. "Aashiq yak'i auranki ne don yana tunanin kema rasaki zaiyi kamar yadda ya rasa matansa na baya sau hud'u yana aure a daren da aka kawo amaren suke mutuwa, wannan dalilin ne yasa yake k'in aure, amman ni ina ji a jikina wannan karan za'a dace insha Allah, zaki iya auransa?" "Kowa zaman jiran mutuwa yake Hajjaju,idan na mutu lokacina ne ya cika, ban jin yadda nake jinsa a raina zan iya rayuwa da waninsa ba, don haka a shirye nake don na auresa." Bari muje ga labarin Aashiq na baya... Lalacewar ciki Garin zogale,rai d'ore garin habbatus sauda, sai a had'asu guri d'aya a cakudasu ana shan cokali daya, safe,rana,dare,a kunu ko koko. [6/11, 11:27 PM] Rabi: 43 Aliyu gogel,haifaffan garin gogel ne,mahaifinsa ya rasu tun mahaifiyarsa Hajjaju na d'auke da cikinsa,shine d'ansu na biyu,amman na farkon ba rayayye ba ne ya rasu tun yana da shekaru biyu a duniya sakamakon k'yanda da yayi fama da ita,Hajjaju ta tsaya tsayin daka gurin tarbiyar tilon d'anta,duk wani tashi fad'i tana yi akan rayuwar d'anta ta inganta, abokansa tun na k'uruciya biyune daga Ibrahim (Baffa Ibrahim) sai Hamza (Baffa k'arami)Abokansa ne k'ush da k'ush,gidajansu yana manne da na juna shiyasa a ko da yaushe zaka samesu a tare sai dai idan Aliyu ya tafi makarantar boko,kasancewar yawancin duk samarin da suka taso d'ai d'aiku ne masu zuwa makarantar boko Aliyu yana d'aya daga cikinsu,kasancewar shima Hajjaju ta tsaya a kansa,to idan ya dawo daga boko makarantar allo da ta dare duk tare suke zuwa,suna matuk'ar k'aunar juna,Aliyu yaso suma a sanyasu a makarantar boko amman mahaifansu sunk'i,saboda hali na rayuwa kuma ba su kad'ai ne a gabansu ba kamar yadda ya kasance shi kad'ai gurin Hajjaju. Hamza yana matuk'ar bak'in cikin yadda rayuwa take garawa Aliyu,babu abinda ya nema ya rasa cikin rayuwarsa,yakan ji dama shine,dama shine hakan ta kasance a gareshi,yana k'ulafucin son yin karatun boko sai gashi bai samu damar hakan ba,duk Aliyu ya tattare damar,amman ya iya b'oye abinda ke ransa ko kad'an bai tab'a nunawa Aliyu ba sai dai ya nuna yafi Ibrahimma k'aunarsa, sai dai kuma soyayya da k'aunar da Aliyu yakewa Ibrahim ta dabance dan ta huce ta aboki da amini dai d'an uwa. Bayan ya kammala secondary school insa sai ya koma zariya da zama hannun yayan mahaifiyarsa, inda aka nema mishi gurbin karatu a jami'a ya fara zuwa cikin sa'a, da yake shi 'ya'yansa duk matane sai namiji d'aya sa'an Aliyun,Bashir (Baffa)da k'yar aka samya gama secondary,irin yaran nanne da basa k'aunar makaranta ko kad'an, gashi mahaifin nasa yana son yayi karatu duk wani burinsa akansa ya d'orasa amman yana kauce masa to zuwan Aliyu sai yayi watsi da shi ya mayar da burinsa kacakom kan Aliyun,musamman da yaga yadda yake da jajircewa akan karatu,sai ya hak'ura da Bashir d'in tunda in ya takura masa ma to bazaiyi abin kirki ba tunda ransa ba ya so,sai suke tafiya kasuwa tare. Duk wani hutu idan ya samu gogel yake tafiyarsa gurin abokanansa, don shak'uwarsu har yau ba ta ragu ba k'aruwa take k'arayi, yanzuma bikin Ibrahim yaje, shine ma yayi masa babban aboki,Hamza ba ya nan ya tafi neman kud'i yadda yaji a bakin Ibrahim d'in. Abinda yasa Hamza tafiya neman kud'i,saboda yarinyar da yake matuk'ar k'auna Zuriyya mahaifiyar Aliyu ta nema mishi auranta,kuma sunyi magana da iyayanta ta fahimta,inda tace ba za'ai bikin ba sai Aliyu ya gama karatunsa kuma suka amince don haka sai ta sanyata a makarantar boko,wannan bak'in cikinne yasa Hamza barin garin,ya tafi neman kud'i don ya nunawa Aliyu ilimi babu tarin dukiya aikin banza ne don haka zaije neman kud'i,kuma zaiyi kud'i don ya nunawa duniya ko babu ilimi ana yin arzik'i. Zuriyya k'anwar Ibrahim ce, kyakkyawa ce ta ajin k'arshe don duk a 'yan matan da suka isa aure a k'auyan babu me kyahunta da kalar birninta, ga ladabi da biyayya wannan dalilin ne yasa Hajjaju ta nemawa tilon d'anta auranta don tana tsoron 'yan matan jami'a, ba tayi nauyin baki ba kuwa da yazo bikin Ibrahim ta zayyana mishi tayi masa natar aure,inda babu musu yayi na'am da wacce ta zab'a masa. Bayan kammala digirinsa na d'aya aka sha bikinsu da Zuriya a lokacin haihuwar matar Ibrahim biyu mace da namiji,Hamza kuwa ko labarinsa ba'a ji, anan k'auyan yabar Zuriya ya koma kano don had'o digirinsa na biyu, da yake a cikin gidansu ya zauna gata ga Hajjaju ba ta da wata matsala sai dai in ya samu lokaci ya dinga zuwar musu. Sai da ya had'a digirinsa na biyu yayi masters kafin ya soma aiki cikin nasara da albashi me matuk'ar tsoka,nan da nan komai ya fara sauya musu kud'i ya zauna masa, da yake mutum ne me alkhairi hatta 'yan k'auyan cin gajiyarsa suke,sai dai har lokacin Allah bai kawo musu haihuwa ba amman suna zaune k'alau abunsu, a lokacinne Hamza ya dawo, babu laifi ya nemi kud'i ya kuma yi d'an karatunsa,sai dai ko kad'an bai kama k'afar Aliyu a gayu da gogewa ba uwa uba dukiyar da ya tafi nemowa don ya fisa, me makon ya saduda amman ina sai ya kuma jin haushi har da tsanar Aliyun ma,duk da yazo ya tarar da yana kula da iyayansa,don har ginin gidansu ya sauya musu, da ya tashi gyaran nasu ne ya had'e har na su Ibrahim aka gyarasa gaba d'aya. A kusan lokaci d'aya Zuriya da matar Hamza Nuriya,da ya aura bayan dawowarsa,suka haihu suka haifi 'ya'yansu duk maza,inda Aliyu yasawa nasa d'an Aliyu,sunan mahaifinsa kenan,shima sunansa yaci zasu dinga kiransa da Aashiq, shi kuma Hamza yasawa nasa d'an Aasad.Haihuwar Aashiq tazo mishi da alkhairai da dama don a yanzu har company yake da shi me zaman kansa, bayan asibitin da ya gina da masallatai duk a garin Zariya don tun fara aikinsa ya d'auko Zuriya suka dawo zariyan,sai dai duk weak end a gogel suke yi, saboda Hajjaju tak'i yadda ta biyosu, acan ma ya gina masallatai,duk wani abu da babu a k'auyan ya kai musu,don haka suke matuk'ar alfahari da shi. Ya gina k'atuwar estate duk da danginsa ba su kasance masu yawa ba yayi ne don Al'ummar annabi,da duk wani d'an gogel da zaizo neman kud'i,kansa tsaye yazo ya samu gida a ciki ya zauna. ya gina gidaje hud'u tanfatsa tanfatsa iri d'aya sak, nasa da na Ibrahim,Hamza,Bashir, haihuwar matarsa uku biyu mata sai namijin sa'an Aashiq me suna Asghar, dukkanin su ukun ya basu aikin da ya dace da iliminsu cikin companynsa, Ibrahim kuwa ya kaishi kasuwa donshi baiyi wani ilimi ba. Bayan ya gina estate sai ya gina gidan marayu, kafin ya kuma yin wani companyn nasa a Abuja,a lokacin Shekarar Aashiq biyar a duniya an haifo masa k'anwarsa mace wacce taci sunan Hajjaju suna kiranta Aaleesha,a haihuwarta ne Hajjaju ta dawo gidan da zama da k'yar,ita tafi son zaman gogel,kamar yadda mahaifan su Ibrahim da Hamza suka k'i dawowa. Hamza da Bashir sun k'ulla ne yayin da suka gano burinsu d'aya ne na son ganin bayan Aliyu,da dukiyar da yake tutiya da ita ta dawo hannunsu, don haka kullum cikin kitsa yadda zasu ga bayansa suke, musamman yadda ya cika zuciyoyin mutane da k'aunarsa ba iya cikin garin zariya ba har gogel gaba d'aya,yana rayuwane domin al'umma ba a cikinsu kad'ai,kullum cikin taimako da cika musu burinsu yake. Al'amarin ya faru ne Aashiq yana da shekaru goma a duniya.. Tsarin haihuwa 1-Idan aka jik'a gishiri da mad'aci aka sha kad'an a watan ba zaa samu ciki ba in Allah ya so hakan. 2-'Ya'yan garafuni,idan aka sha guda uku to a wannan shekarar ba za'a samu ciki ba, ko kuma a daka ayi insertin da shi za'a dace in Allah yaso hakan. 3- A miki laya da ganyan na'a na'a, idan kina tare da ita ba za ki d'au ciki ba, sai dai in rabo ya tsago. 4- Kuna gama saduwa ki mik'e tsaye ki lashi gishiri ki tsalle. Ki saka a ranki komai nufi ne na Ubangiji. [6/13, 9:01 PM] Rabi: 44 Abuja suka tafi da shi da Bashir da Hamza,kafin tafiyarsa da k'yar suka rabu da Aashiq,mak'ale masa yayi sai ya bisa don yafi k'ulafucinsa akan mahaifiyarsa ita kuma Aleesha tafi k'ulafucinta. A ranar sukayi abinda zasuyi suka juyo saboda fitar wuri sukayi don su daho akan kari,sun kusa shiga zariya al'amarin ya faru, akuya kawai ya gani a gabansa bai san daga ina ta fito ba,saura kad'an yabi ta kanta yaja wani irin birki wanda har yayi tunanin tayarsa ta samu matsala ya fito don ya duba ya gani,wasu mutane ya hango sun taho da makamai a hannunsu, cikinsa ne yayi wani irin k'ugi ya nufi motar a gigice yana jan murfin sai ya jita a kulle,a rikice ya kalli su Hamza da ke cikin motar yace. "Ku bud'e mini,mu gudu wasu mutane ne suka taho." Yana maganar yana waigawa yana kallon mutanen sun kusa zuwa dab da inda yake,tuni tsoro ya gama mamaye zuciyarsa. "Ku bud'e mini don Allah, sun kusa taddani." Babu wanda yace d a shi k'ala kamar gumaka haka suka zama,cikin raunin murya da sarewa yake cewa. "Bashir,Hamza abinda zakumun kenan,me nayi muku da zaku aikata mun hakan?" Sai a lokacin dabarar guduwa tazo masa amman ina sun riga da sun cimmashi,wani k'aton k'arfe suka d'aga suka k'wala masa a kansa. "Iyalina,ku kulamun da Aashiq." Itace kalmarshi ta k'arshe kafin ya fara kalmar shahada,jina jina sukayi masa,kafin Hamza da Bashir su fito daga motar suna jinjina musu,kana suka yiwa motar kwatsa kwatsa yadda zai nuna hatsari yayi, kafin su d'au wayarsa da itama suka yi mata kwatsa kwatsa,suka kira Ibrahim suka sanar masa yayi hatsari bayan sun kira police sun kwatanta musu gurin,kana suka bar gurin bayan sun tabbatar ba su bar shaidar komai da zai tona asirinsu ba. Mutuwar Aliyu ta gigita mutane da dama, Aashiq kuwa duk k'arancin shekarunsa mutuwar ta tab'asa fiye da zaton masu zato,don a lokacin yasan mutuwa ya kuma san me ake nufi da mutuwa, Ibrahim kuwa sam zuciyarsa ba ta aminta da hatsarin da Aliyun yayi ba,haka kawai yaji kamar da saka hannu a ciki,musamman yadda suka tafi tare da su Hamza ya akai suka barshi ya taho shi kad'ai,amman kawai dai sai yaja bakinsa yayi shiru.A haka rayuwa taci gaba da tafiya sun karb'i rashin Aliyu sun dangana,amman Aashiq sai da aka dinga yi masa rubutu kana aka samu ya dawo dai dai, Hamza da Bashir duniya tayi musu dad'i su suke juya dukiya yadda suke so,yayin da maaikata suka fara ganin ba dai dai ba.Bayan Zuriya ta fita daga takaba Hamza ya fito fili ya nuna yana son auranta ko don ya rik'e amanar da d'an uwansa ya bari, a cewarsa,inda Zuriya ta nuna ba za ta auresa ba sai ya biyo mata ta sama ,inda iyayanta suka tank'warata suka nuna mata muhimmancin auran nata don dole ta aminta za ta auresa yayin da kishi yasa Nuriya ta zuba mata guba a abinci wacce ta k'one mata jini gaba d'aya ta rasu,ko da akaje asibiti likitan yace zuciyarta ce ta buga,da yake sun had'a baki da Nuriya don gudun kar aji guba ce a shiga bincike asirinta ya tonu, a lokacin idan kuga Aashiq sai ya baku tausayi, d'an k'araminsa da shi ya d'an d'ana d'acin rashin mahaifa, d'acin da yake ji a zuciyarsa wanda ya tsinci kansa a irin halin da yake ciki ne kawai zai fuskanta yafi tausaya masa. Bayan mutuwar mahaifansu shi ya zamo uwa ya zamo uwa gurin Aaleesha da shi kad'ai take yadda, tare zasu je makaranta su dawo, to sai Aasad shima tana d'an yadda da shi da yake duk makarantarsu d'aya.Aasad zuciyarsa irin ta mahaifinsa ce akwai bak'in ciki da hassada, don yana mugun jin haushin yadda kowa yake nuna k'auna da kulawarsa akan Aashiq, hatta mahaifansa da kakanninsa, gashi duk jama'ar estate in kowa yafi k'aunarsa, haka a makaranta ma yafi shi k'ok'ari da jama'a, gashi mayan k'wallo indai suna buga wasan k'wallo sai ya cinyesu, shikwa Asghar bai d'auko zuciyar mahaifinsa ba, da zuciya d'aya yake k'aunar Aashiq,k'auna irin ta jini,gani yake Aashiq in ya can canci a nuna masa soyayya da kulawa fiye da wacce ake nuna masa a yanzun. Hajjaju,Aashiq da Aalisha take kalla taji sanyi a ranta, taga kamar Aliyunta take gani, don Aashiq bai baro komai a kammannin babansa ba.Bayan ya kammala secondary school insa ne kuma yak'i karatu sam,inda ya mayar da hankalinsa gurin buga wasan k'wallonsa, Hamza ne ya shiga ya fita ya juyar masa da hankali daga karatu, don gudun kar yayi karatu nan gaba yazo yafi k'arfinsu, sai dai abinda bai sani ba Aashiq k'waro ne a compuiter, yasan cumpuiter ciki da bayanta, kuma irin gifted in nanne suka ga abu sau d'aya sun d'aukesa har abada. A haka rayuwa taci gaba da tafiyar masa har ya fara fita k'asashen waje buga wasan k'wallo,duk da ba a son ran su Hamza ba,don sun so hana sa Hajjaju tace a barsa tunda yak'i karatun in ya zauna a gaban nasu me zaiyi, cikin nasara ya fara buga wasan k'wallonsa nan da nan yayi suna ya shahara, jikinsa yayi wani irin murd'ewa alamun k'arfi suka bayyana a garesa,kud'i suka zauna masa, sai ya zamto ba kasafai yake zuwa nigeria ba tunda suna video call da Hajjaju da Aaleesh, don Aaleesha ta fara zama budurwa kuma Aasad yana kular masa da ita yadda ya kamata, don shak'uwa ce sosai tsakaninta da Aasad in,wacce ta zarce musu soyayya ba tare da sun sani ba. Yana da shekaru 25 amman in ka gansa ba za kace shekarunsa haka ba, ya zama cikakken namiji kyahunsa da gogewar fatarsa sun k'ara bayyana, farine tas, sumar kansa da sajansa da gemu ne kawai bak'i a jikinsa sai k'wayar idanunsa, kyahunsa ne shiga cikin idone ya zauna daram sai kayi da gaske kafin ya fita, turawa da hausawan da ke zuwa duk suna kawo kansu garesa amman bai jin zuciyarsa ta shirya bud'ewa duk da yana jin lokacin yin auransa yayi don mabuk'aci ne shi sosai a yadda ya karanci halittarsa,yana samun wacce hankalinsa ya kwanta da ita kawai zaiyi wuf da ita ya huta. Maryam,itace k'addarar ta fara biyowa ta kanta,'ya ce gurin Baffa Ibrahim, wan mahaifiyarsa kenan kuma aminin majaifinsa, sun dai daita kansu ne a wani zuwa da yayi, dama ita can tana k'aunarsa, ai tunda su Hamza suka ji Aashiq zaiyi aure hankalinsu ya tashi, ta yaya zasu bari yayi aure su da suke son ganin rayuwarsa ta wulak'anta,idan suka bari yayi aure dukiyar da suke ganin ta zamo,tasu kenan ta tashi a banza. don haka sukayi tsafin da muddun ya auri mace a daren da aka kawota za ta rasu, ta nanne za'a fara hanasa aure daga nan sai su ruguza rayuwarsa, don vazai yuhu su kashesa ba shakku zai shiga zuciyar mutane,musamman masoyan babansa da har yau suke k'aunarsa. A daren kuwa da aka kawowa Aashiq Maryam ta amsa kiran mahaliccinta, ya shigo yana d'oki, yana zuwa ya tarar da ita a sank'ame,tashin hankalin da ya shiga bazan iya zayyana muku shi ba, a ranar sadakar bakwanta Baffa Ibrahim ya kuma d'aura musu aure da k'anwarta Zaleeha,itama kamar yadda yazo ya tarar da Maryam haka ya tarar da ita,tashin hankalin da ya shiga zato ma ba zai tab'a baku shi ba, yayin da Baffa Ibrahim da matarsa suka karb'i k'addarar da ta samesu ta rasa 'ya'yansu hannu biyu, har sukaji inama suna da wata 'yar da ba ta da aure bayan Zaliha su k'ara masa, inda Aashiq ya hak'ura da auran ya tattara ya koma yaci gaba da harkar k'wallonsa amman sai da ya memi maganin da yake kwantar masa da sha'awarsa in ta motsa. Huda,itace ta uku,'yace gurin Baffa k'arami (Hamza)Ita ta kafe sai ta auresa babu ta inda bai biyo mata ba akan ta hak'ura da shi amman ta k'i,inda mahaifiyarta ta goya mata baya, ita kuma hak'on dukiyar da Aashiq in yake da ita take, ganin bashi da wata mafita yasa ya gaya mata tsafin da suka yiwa Aashiq in inda karaf a kunnan Baffa Ibrahim, baice da shi komai ba ya fara nemawa Aashiq magani,sai sukayi asirin da suka mayar masa da hankalinsa k'auye,inda ya kwashe iyalinsa suka koma can da zama, ba tare da ya k'ara wani yunk'uri akan Aashiq in ba. Ko kad'an sun kasa tank'wara Huda akan ta hak'ura da Aashiq tak'i, tace ita ko mutuwa za tayi bayan ta auresa ta shiryawa hakan... kisamu ganyen gwaiba me dan yawa kidafa ya dafu sosai ranar da kika fara jinin haila zaki dafa seki maidashi kamar ruwan shanki har tsawon kwana hudu duk abunda ke cikin maraki insha Allah ze futa du wani datti dake cikin mahaifa da mara yana maganinshi kuma ciki ze iya shiga bayan kinyi wankan haila da yarda Allah Kuma wanan nayishi wly kuma naga anfaninshi. Ki sami alo vera ki matse ruwanta ki had'a da man zaitun kiyi insertin,yana maganin sanyi yana kuma matsi.yi da shi kikai tasha za'a dac[6/15, 8:32 PM] Rabi: 45 Mahaifin Baffa K'arami ne ya tsaya kai da fata sai anyi bikin Aashiq da Hudah,inda hankalin Baffa k'arami ya tashi ya shiga k'ok'arin karya tsafin da ke jikin Aashiq in,sai dai ba'a yiwa Allah dabara, kamar yadda su Maryam suka tafi haka Hudah tabi bayansu,bayan an d'aura auranta da Aashiq an kaita gidansa,yayin da Baffa k'arami yayi kuka ba kad'an ba saboda yana mugun son Hudah,hakama mahaifiyarta da Aasad,duk sun d'orawa Aashiq alhakin mutuwar Hudan,suna ganin kamar shine ya ja hakan,tunda Baffan ya sanar musu ya karya tsafin,shiyasa suka kuma k'udirar bak'ar aniya akan Aashiq in.Mahaifan Baffa k'arami kuwa ji sukayi dama suna da wasu jikokin sui ta k'ara masa har sai komai yazo k'arshe,don jinin Aliyu ba abun k'yamata ba ne a gurinsu.Aashiq kuwa tattarawa yayi ya hak'ura da auran gaba d'aya,ko auran Hudan ma don anfi k'arfinsa ne kafin kuma Faleesha ta shigo rayuwarsa. Bayan wasu shekaru,Aashiq ya k'ara shahara a fagen buga wasan k'wallo ya tara kud'i na ban mamaki don a lokacin duniya shi take yayi,kafin suna buga wasa wani yayi masa wani irin duka ya fad'i ya samu matsala a k'ashin k'afarsa,wanda dan dole ya hak'ura da wasan k'wallo,tunda ko tafiya ma sai da taimakon sanda yake takawa sosai,yayin da suka yi mishi sallama da dalolin Africa inda ya tattparo ya dawo gida gaba d'aya,ganin tarin dukiyar da yake da ita kuma babu wani amfani da za tayi masa yasa ya fara aikin Allah da ita, ya fara rayuwa irin wacce mahaifinsa ya tafi ya bari,don tun yana yaro yakan ce masa. "Turaki,rayuwa don al'umma itace rayuwa,ba rayuwa a cikinsu ba,duk irin mutanen da suke d'aukar matsalarsu ita kad'aice matsala,to tabbas tunaninsu tsukakke ne,wa'yanda kwa ke d'aukar matsalar al'umma itace tafi shafarsu to shakka sune masu k'aunar al'umma,kada ka damu da buk'atarka kai kad'ai ka damu da buk'atar ko da mutum d'aya ne." Ya manta da kansa ya mayar da rayuwarsa ba komai ba,ya mayar da rayuwar alumma itace rayuwa,ba iya kad'ai garin zariya ba,har k'auyuka yake sakawa a binciko masa,duk k'auyan da ke buk'atar tallafi yakan bayar aje a tallafa musu,ya bada jininsa a bawa mabuk'ata,ziyartar gidan marayu kuwa ya mayar da ita al adarsa,ba kuma iya gidan marayun da mahaifinsa ya gina ba,dukkanin yaransa da ke tare da shi,rayuwarsu ya tallafa ya janyo su jikinsa, daga masu shaye shaye sai almajirai da marayu. Falisha,Nabila,Ramla,Rabi'ah,Farida,dukkaninsu sun bud'i ido ne sunga suna rayuwa ba tare da sun san waye yayi silar zuwansu duniya ba,junansu kawai suka sani,tare suke tashi su fad'i,daga wannan kango zuwa wannan kango suke rayuwa,suna rayuwa ne gwanin ban tausayi domin sai sun fita sunyi bara sannan zasu samu abinda zasu sakawa cikinsu,an nemi keta musu haddi kusan sau nawa Allah ne kawai yake kub'utar da su, a yawon bararsu suka had'u da Baba Azumi,itama barar take fitowa da k'aramar 'yarta,Faiza,mijinta ne ya gudu ya barta,bayan shi yayi silar zuwanta garin ba ta san kowa ba yayin da aka koreta daga gidan hayar da take ciki, ya zamto sai tayi bara za ta samu abinda zasu saka a bakinsu ita da 'yarta, had'uwarsu sai suka zamto tamkar wani ahali,sukewa Baba Azumi kallon mahaifiyarsu, har suka dawo kwana cikin kango d'ayap babu wanda ya kallesu da idan rahama ya tausaya musu,ya nuna suma 'ya'yane ya tsaya dominsu sai Aashiq. Tsautsayi ne yasa ya kad'e Faleesha,yayin da suka d'auketa suka kaita asibiti,satinta guda kafin ta san inda kanta yake,kafin ta samu ta farfad'o,bayan taji sauk'i suka d'aukota don kaita gidansu,inda tayi musu kwatancan kwangon da suke ciki, suna ganinta da gudu suka rugo suka rungume juna, ko wacce da hawaye a fuskarta,sunji tsoro sosai,har sai da suka ji rayuwar sam ba dad'i rashin Falisha tare da su, ta d'an girmesu sai suke mata kallon yayarsu, yayarsu d'ince ma don basu da kowa sai junansu. "Munji tsoro,ashe zaki dawo garemu?" Cewar Rabee'ah,yayin da Ramla tace. "Dama Baba Azumi tace mana zaki dawo." "Zan dawo,mutuwa ce kawai za ta hanani dawowa gareku." "Oga ina tunanin fa marayu ne yarannan." "Idan suna buk'atar kyakkyawar rayuwa,kace da su su shirya zaka dawo ka tafi da su." Basu da wani zab'i illa na bin Khalil yakaisu duk inda zai kaisu, sun gaji da gaske har cikin zuciyarsu da bin kwangaye ana korarsu wasu na neman keta musu haddi. Hajjaju sam ta nuna baza ta zauna tare da su ba,akwai gidaje da yawa dake cikin estate in ba ta hana ya kaisu can ba, haushi yasa shima ya koma can da zama yayin da Aaleesha ta biyosa,don rayuwa a inda babu Yayanta ta kan jita kamar ba rayuwa ba, tafi son ta shak'i irin iskar da yake shak'a Cikin kwanaki kad'an rayuwarsu ta sauya,farin ciki ya gudana a zukatansu kafin Baba Hadiza ta shigo rayuwarsu,suka mayar da kansu Ahali guda,don dukkaninsu junansu zasu nuna su kira danginsu. Tun a gani na farko da Falisha ta yiwa Aashiq zuciyarta ta fara doka masa,kafin ta fara karb'ar sabon yanayi a kansa,saboda samun kusanci da shi take shishshigewa Alisha,idan Alishan za ta gyara masa d'aki tare suke yi,abinci ma in zata kai mishi tare zasu kai,psai dai ko kallo ba ta isa a gurinsa ba,yayin da soyayya da k'aunarsa suke k'ara k'arfin gudu a zuciyarta har ta kasa jurewa ta ajiye ajinta a gefe tare da kunya da akan san 'ya mace da ita da kawaici ta tareshi akan tana son kusancin zuciya da tasa zuciyar kai tsaye yace da ita. "Kinyi kuskuren barin zuciyarki ta so kusanci da tawa,don abune wanda ba za ta samu ba,don ni da aure tuni k'addara ta saka almakashinta mai k'arfi ta datsa tsakaninmu." "Ni ina sonka,ina son kasancewa da kai,ina son tafiya tare da kai,ina son tayaka jin rad'ad'inka da sauke hak'k'inka,amman duk da haka kana ganin kuskurena,ka bamu matsuguni,mabuk'ata ka ciyar da su,marasa muhalli ka basu,ka d'aukeni a matsayin marainiya ka bani muhalli a zuciyarka nima don Allah." Idan aka bashi labarin akwai lokacin da zuciyarsa za ta bud'ewa wata ba shakka zai k'aryata hakan,sai gashi bai san lokacin da har ta bud'ewa Falisha ba,ta fara motsawa da doka mata,yayin da sanyayyar soyayya ta fara gudana a tsakaninsu duk da yana jin tsoro,yana jin tsoron abinda ya samu su Maryam ya faru da ita,har aka fara shirin bikinsu a tsorace yake,ba kuma abun yace ya fasa ba,tare aka had'e bikin nasu da na,Ramla da Asghar,da suka had'e kansu suma,Rabee'ah,Farida,Nabila su kuma a cikin yaran Aashiq ne sukai wuf da su, sai na Aalisha da Aasad, ta kammala karatun nata,inda ta karanci fannin jarida,dama Aashiq ne ya hana auran nasu sai ta gama karatunta,tunda shi bai samu damar hakan ba,ba suji komai ba tunda Falishan mace ce,kuma hannunsu za ta dawo,tunda Aasad ne zai aureta sai yadda sukayi da ita. Maganin Infection 1-Zuma,garin tafarnuwa,garin zogale,garin habbatussauda,kustul hindi,ki had'asu guri guda ki kwab'a da zuma,kina shan 2spn sau uku a rana,insha Allah zaki rabu da shi. 2'Ya'yan zogale,kina shan guda d'aya kwana7 3Bagaruwa garin hulba zaki had'asu ki tafasa kina zama a ciki sau 4 a rana 7days. 4-Man habbatus sauda,kina sha kina inserting.Manzon Allah (S.A.W)yace."Habbatul baraka ta isheku magani akan komai banda tsufa da mutuwa." [6/20, 7:53 PM] Rabi: 46 Bayan an d'aura auransu Aashiq zamewa yayi ya komo gida,tun kan ya k'araso yake kiran wayar Falaisha yace ta sameshi a d'akinsa,daran jiya ne sam bai rintsa ba saboda azabar ciwon mara,har zuwa safiya ma sam bai rabu da azabar da yake ji ba,abar tasa ma tak'i kwanciya bare ta risina masa,bai jin zai iya kaiwa har dare a haka,tunda an d'aura ta zamo halaliyarshi ai an gama magana. Tana shirin fitowa daga bedroom in,saboda ba ta ganshi a ciki ba,suka ci karo shi kuma zai shigo,hannunta ya rik'e suka k'arasa ciki a tare ya zaunar da ita bakin gado kafin ya nufi gaban mirro yana ajiye hular da ke hannunsa,had'e da cire agogon hannunsa ya ajiye,kana ya zare babbar rigar da Asghar ne ya matsa masa sai ya saka,saboda anko sukayi duka su ukun.Kanta yana k'asa har ya gama cire kayan jikinsa tsaf yayi saura daga shi sai gajeran wando kafin ya k'arasa ya sakawa k'ofar key,gabanta ne yayi wani irin fad'uwa ta d'ago ta kalleshi,da sauri ta kuma yin k'asa da kanta,a ranta tana fad'in."Maza sam basu da kunya wallahi"Ga k'arfaffan jikinsa da ya kuma tsoratar da ita tunda ba tab'a ganinsa tayi a wannan yanayin ba. Tausayi da k'aunarsa sun raunata mata zuciya,ba za ta iya hanashi kanta ba,don haka ta jurewa komai,duk da taso ya bari a kaita saboda kunyar mutane,amman yanayin da ta ganshi sai taji ta shiryawa jin kunyar ko waye matuk'ar za ta nemawa mijinta lafiya tunda ba zina taje tayi ba. Duk da kasancewar a buk'ace yake,bai bari notin kansa sun kunce ba yabi da ita a hankali yadda ba za ta wahala sosai ba. Wayar Aasad ce a hannun Alisha tana dannawa,hotuna suka gama yi ya mantata a hannunta ya tafi,message ne ya shigo wayar daga saman ta fara karantawa. "Akwai matsala fa,tsafin nan bazaiyi aiki akan Falisha ba." Sai gashi kamar an jefosa yazo ansar wayar,bashi tayi tana tattauna message in a ranta kafin ta tashi tabi bayansa, tana fita yana shiga mota,a hannun Khalil ta anshi key in motar Aashiq ta shiga tayi saurin bin bayanshi. Gidansa da ba kowa ne yasan da zamansa ba ta nufa,acan yake sharwoliyarsa da 'yan mata kala kala,bai lura da message in da aka turo masa ba har yaje gidan,Alisha kuwa daga nesa tayi parking in motarta bayan ta hango gidan da aka bud'e masa ya shiga da motarsa,sai da ta bari ya d'an jima da shiga kana taje tayi knocking in gate in gidan,ganin mace ce yasa me gadin bai hanata shiga ba,kai tsaye kamar ta san kan gidan ta kutsa kanta ciki.Yana shiga Baby ta taho da gudu ta shige jikinsa,rungumeta yayi tsam a jikinsa don yana samun yadda yake so a gurinta,shiyasa ya killaceta yake amfani da ita shi kad'ai,babu wani sirrinsa da ba ta sani ba,hatta auran da aka d'aura masa ta sani,ta kuma san auran manufa ne ahiyasa ba ta d'aga hankalinta ba,duk da tana kishinsa sosai,a dai dai lokacin wayarsa tayi ringing ya cirota daga aljihu,Baffa K'arami ne ke kiransa da sauri yayi peaking. "Kana ina ne,ba kaga message in da na turo maka ba?" "Ban lura ba gaskiya." "Ok,cewa nayi akwai matsala,tsafin bazaiyi aiki akan Falisha ba,yanzu yaya zamuyi?" "Za'a samu wanda zasu kasheta a daren da aka kaita itama,na tabbata daga kanta babu wata mace da za ta k'ara gigin auransa." "Tom shikenan,na bar komai a hannunka" Ji yayi kamar k'arar rufe k'ofa,yana waigawa Alisha na barin gurin da gudu,ta riga ta gama jin wayar da yayi,ta kuma ganshi rungume da mace,bai san sanda yayi wurgi da Baby dake jikinsa ba yabi bayan Alisha da gudun tsiya,wani irin gudu take cikin tashi hankali tana kuka har ta isa bakin motarta ta shiga ta jata da gudun gaske, Aasad na ganin ta shiga mota shima ya dawo ya shiga tasa motar hankalinsa a matuk'ar tashe yabi bayanta,wani irin gudu take na fitar hankali,ji takeyi kamar tayi tsuntsuwa ta ganta gaban Yayanta,ba ta tab'a da na sanin fita babu waya irin yau ba, ji takeyi kamar ta cire zuciyarta ta wullar ta d'auki wata sabuwa ta saka a k'irjinta,don zuciyarta tayi kuskuran son Aasad,sam bai dace ta soshi ko kad'an ba,duk da yanzun ma jin muguwar tsanarsa take wacce ba tasan ainihin daga inda take fitowa ba,burinta kawai a yanzu auransa dake kanta ya sauka a yau d'in da aka d'aurasa,idonta ya rufe gudu kawai take shararawa ba ta lura da daf in da ta taho ba kawai ta kutsa kai,aikwa ta daki motar tata ta hantsila ta kuma hantsilawa. Jina jina aka d'auki Alisha aka nufi asibiti da ita,sai dai kan a k'arasa ma ta cika,hankalin Aasad ya tashi fiye da na da,don yana matuk'ar k'aunarta ita ta fara bid'e zuciyarsa kuma ita kad'ai zuciyar take nunfasawa,biyotan da yayi ma da ace ya kamata to ba wani abu zaiyi mata ba,d'auketa zaiyi har sai yasa an rufe bakinta kafin ya saketa,ashe ma ita duniyar za ta bari gaba d'aya, amman hakan baisa imani ya shiga zuciyarsa ba saboda an zareshi. Gaba d'aya estate in ta hargitse daga hidimar biki an koma zaman makoki,har akayi sadakar uku Aashiq ga shinan ne dai bai san me yake masa dad'i ba,duk wani bincike anyi an kasa gano dalilin barin Alisha gidan,Aasad har da kwanciya ciwon k'arya ko don d'auke zargi daga kansa, don Khalil yace yana tunanin bayansa ta bi,don yana fita itama ta fita. Ana sadakar bakwai ko wace amarya aka kaita gidanta,Falisha da Ramla su a cikin estate inne,su Rabee'ah kuma ba ciki mazajansu zasu zauna ba. Har lokacin Aashiq gashinan ne kawai,ji yake duniyar ta kuma yi masa fad'i sosai,yana ji tamkar shi kad'ai ya rage a cikinta,amman yana d'an jin sanyi idan ya tina yau kwanansa bakwai da aure babu abinda ya samu matarsa,duk da rabon da ya sanyata a ido tun ranar da ya anshi budurcinta,yana nan yana jinyar rashin Alisha cikin duniyarsa. Sagir,yana d'aya daga cikin yaran Aashiq,mutum ne ma'abocin d'aukar hoto, a ko da yaushe ba ka rabasa da camera,wasu mutane yaga sun shiga cikin gidan da aka kai Falisha,kawai yaji zuciyarsa ba ta aminta da su ba,ba tare da tunanin komai ba yabi bayansu,yana kuma rik'e camrar da ke hannunsa,sanda ya shiga sun riga sun shiga d'akin da Falisha ke ciki,kuma yaji k'arar saka key don haka yayi saurin zagawa bayan d'akin inda window yake, sai da ya taka benci tsayinsa yakai kana ya lek'a,sun d'ad'd'aure Falisha,sun nane mata baki da flasta,kana suka fara amfani da ita,duka su hud'un sai da kowa yayi amfani da ita,tana kuka tana mutsu mutsun azaba, kana suka murd'e mata wuya suka kunceta suka gyara komai tsaf,yadda ba za'ayi zargin komai ba,suna k'ok'arin fita suka ji kamar dirgawar mutum,Sagir ne ya dirga bayan ya gama d'aukar komai a camerarsa,yayin da su kuma suka yi saurin ficewa gudun kar asirinsu ya tonu. Aashiq kuwa yana can asibiti da Hajjaju bata da lafiya,tun daga mutuwar Alisha jikin nata ya kuma rikecewa,da wannan damar suka samu sukaje suka kashe Falishan, dare ya raba sosai suka dawo,sai da ya raka Hajjaju har d'akinta kana ya nufi gidansa,dama tun d'azun hankalinsa ke kan Falisha yana ta kiran wayarta ba ya tafiya,ga wani irin yanayi na fad'uwar gaba da yake jin kansa a ciki,yana bud'e d'akin yayi tozali da Falisha a sank'ame,baya kawai yayi ya zube anan gurin nunfashinsa ya tsaya cakk,Khalil ne ya biyo bayansa da ledojin da suka taho da su ya tarar da shi cikin wannan yanayin. Sun sanarwa da Aasad cewar sunji dirar mutum,suna tunanin wani fa ya gansu, inda yace su dai zuba ido suga zuwa washe gari,Sagir kuwa ya rasa wa zai tunkara da vidion da ya d'auko,hankalinsa gaba d'aya a tashe yake,Aashiq kawai yake so ya gani,don bai san waye yake shirya masa munak'isar ba,Washe gari da safe mutuwar Falisha ta fasu,hankalin kowa ya tashi musamman su Ramla,sunyi kuka kamar ba gobe,Aashiq kuwa tunda aka d'auke shi aka fita da shi bai san wanda ke kansa ba har yanzu. Sagir suna hira a tsakaninsu suna jajanta yadda rayuwa take zuwarwa Aashiq,inda d'aya daga cikinsu yake cewa. "Ba dole Oga ya shiga d'imuwa irin haka ba,ace sau hud'u yana aure suna mutuwa,gashi wannan tsiransu kwana bakwai da k'anwarsa." "Kai dai bari,ina jin dama a raba rad'ad'in da yake ji aban rabi ko zan rage masa nauyin da yake zuciyarsa,rayuwarsa tanabani tausayi,ya tsaya dominmu amman shi kan babu wanda ya tsaya dominsa." Cewar Khalil,yayin da Sagir yace. "Mune muka tsaya dominsa,na tabbata duk cikinmu kowa zai iya bada rayuwarsa dominsa,insha Allah komai ya kusa zuwa k'arshe,duk masu neman ruguza rayuwarsa k'arshensu ya kusa zuwa." "Saboda me kace hakan?" Suka tambayeshi a kusan tare. "Saboda matansa da ke mutuwa ba haka kawai suke mutuwa ba kashesu a ke." "Kai wa ya gaya ma haka?" Cewar Khalil,yayin da Sagir yace."Ina da hujjar hakanne,farkawar Aashiq kawai nake jira." Saminu shine ya sanarwa da Aasad tattaunawar da sukayi da Sagir,saboda dama yaron Aasad inne ya shigo jikin Aashiq don samun wasu bayanan,inda Aasad ya tura wa'yanda suka kashe Falisha su kasheshi bayan sun karb'i camerar da ke hannunsa,da fari sacesa sukayi suka gana masa azaba iri iri,amman yak'i gaya musu inda camerar take,k'afarsa da kafad'unsa duka harbi ne amman yak'i fad'i,don ya shiryawa mutuwa akan dai ya gaya musu inda ya ajiye camerar,wayarsa suka kunna,suna kunnawa kira na shigowa. "Mutumina wai ina ka b'uya ne,ko rashin lafiyar Ogan naku ce ta b'oyeka?ina ta neman layinka ban samu ba so nake ka gayan password in camerarka zanyi amfani da ita" Cewar abokinsa Naziru,babu halin magana,sun toshe masa baki,cizo ya gartsawa wanda ya rufe masa bakin da k'arfi yace. "1997,ka gudu,ka dank'a camerar hannun Aashiq ko Baffa Ibrahim" Suna ta k'ok'arin kashe wayar tak'i kasuwa sai da Naziru yaji bayanin Sagir,inda takaici yasa suka harbe Sagir nan take, suks hau tracking number Naziru, shikuwa ya bud'e camerar yaga ta'asar da ke ciki,yana shirin barin gidan yaji dirar mota,don haka ya d'au takadda yayi rubutu,yana fatan k'arshen wa'yannan azzaluman yazo k'arshe,ya samu ya sirare bayan sun d'an fafata sun harbeshi a k'afa da kafad'a,kafin bulet insa ya k'are, shine ya yanka ta cikin kasuwar su Baba,da shi yaji ya aminta shine ya ajiye masa camerar, kafin su bi bayanshi su kashe shi. Daga nanne rayuwar Aashiq ta ruguje ta lalace,ya zamto ko kad'an ba ya iya rintsawa daga dare har rana,yana rayuwa ne kawai ga shinan kamar matatce,da wannan Aasad yayi amfani ya d'ora masa kwalbar giya a hannu da cocain,tunda ya fara amfani da su yaji yana samun bacci yadda ya kamata shikenan ya koma rayuwa sai da su,musamman yadda ciwon mararsa ya k'ara k'arfi,inda likita yace da shi tunda ya riga yasan mace maganin bazai d'aukeshi ba sai dai allura,ita kuma za ta iya bashi matsala,shiyasa da yaji ciwon zai motsa zai d'ad'd'aki giyarsa sai ya make ya hau bacci,dalilin da yasa shan giyar tasa yayi k'arfi kenan,Asghar sam bai so Aashiq ya fara shan giya,inda ya shiga k'ok'arin ganin ya rabasa da shan giyar,to hakan sai ya dinga kawo sab'ani tsakaninsu,Aasad kwa ya dinga jin dad'in hakan,ya so ya dilmiyar da shi harkar bin mata,saboda yanzu ya daina b'oye shan giyarsa da neman mata,dama saboda Alisha yake b'oyewa yanzu kuwa tunda ba ta duniyar sai ya samu sakewa,amman sam yak'i,ya nuna ba ya sha'awar hakan da yana da damar hanasa shi kansa da ya hana shi. Cigaban Labari.. [6/21, 2:12 PM] Rabi: 47 Su Baffa Hajjaju ta kira akan maganar auran Nusrat da Aashiq,dama suma suna shirin zuwar mata da maganar,don sun tabbatar da karuwar ya ajiye a cikin gidan,shiyasa zasu yiwa tufkar hanci suyi musu aure ko da kwa ba ya so,in yaso ana auran ta mutu sai ya koma gidan jiya,to sai gashi Hajjaju ta fara musu maganar da kanta,inda ta basu address in gidansu Nusrat da ta karb'a a gurinta,suje su nemo auranta tare da kai kud'i,kuma ta nuna ba ta son a ja wani lokaci,suma kuma dama ba zasu so lokacin auran yayi tsayi ba. Ko da sukaje Baffa Shamsu suka samu da maganar sunzo neman auran Nusrat ne,inda mamaki ya cikashi yace. "Ikon Allah ashe kuna da labarinta,amman ba ku da labarin ta tab'a yin cikin shege ta zubar?" Baffa K'arami ne yace. "Ai ko haihuwar d'an shege tayi,a hakan zamu nemawa d'anmu auranta." Jinjina kai Baffa Shamsu yayi,kafin yace. "Dama na gaya muku ne kada daga baya kuzo kuce ba ku san zancan ba." Dubu d'ari biyar suka bayar kud'in auranta,ba tare da sunji komai ba,saboda kwalliya ce za ta biya kud'in sabulu,sun tsayar da rana,nan da sati biyu,Baffa Shamsu ya nuna lokacin yayi huri,amman sukace baiyi ba,don basa buk'atar ko tsinke daga garesu. Baki washe yaje ya sanarwa da Iya alkhairin da ya samesu,don shi ba murnar auran Nusrat in yake ba,murnar samun kud'in yake,don samunsa yayi k'asa sosai,an zaftare musu albashi,ga kuma lasha money a tare da shi,duk abinda ya samu ta kwashe ta kai gidansu,inma 'yan yankan kaine ta samo can ta jiyo,ai sai Iya ta fishi murna,fad'i take. "Allah sarki,'yar baiwar Malam tana can,shiyasa nace Shamsu ka rabu da ita kada ka koreta daga gidannan kak'i jin maganata, ga shinan ta samo arzik'i za ta cishi ita kad'ai,ka cuce ni ka gama da ni Shamsu." Sai ta fyace majina tana gurshek'an kuka kafin ta cigaba. "Bani dukiyar auran jikata nan,na rik'e,ni yafi can canta da na karb'a,tunda mahaifinta ba ya raye,Allah sarki Audu bawan Allah,Allah ya jik'anku kai da Maimuna kun iya haihuwar irin arzik'i." "Ai ko Audu da Maimunan za ki saka su dawo duniya,babu wanda ya isa ya anshi kud'in nan a hannuna." "Idan ba su dawo duniyar ba,sun bar wacce ta isa ta ansar musu." Cewar Yusra tana kallonsa had'e da k'ank'ance idanuwa,waya sukayi da Nusrat take gaya mata,yau za'aje gidansu kai kud'in auranta,fargabarta kada a gaya musu k'azafin da akayi mata,shine Yusran tace bari taje gidan ta gani,to ta dad'e a bakin k'ofar d'akin Iyan duk taji abinda suke fad'e. "Yauwa d'iyar albarka gara da kika zo,don idan ya rik'e kud'in nan a hannunsa lasha moneyn matarsa ce za ta lashe alqur'an,gara ki ansa ki bani,tunda nice dolenku ni nayi silar zuwan mahaifinku duniya." "silar zuwan Mahaifinmu kikace,amman ba silar zuwan Yayarmu da Yusra ba,don haka dukiyarsa kad'ai ta halatta ki ci ba ta mu ba,kai kuma ka bani kud'in nan na tafi,don shi ya kawo ni,ba dukiyar auran Amima bace bare ka saki baki ka rik'.." Ba ta k'arasa ba ya d'auketa da mari. "Ko ubanki yayi kad'an ya karb'i kud'in nan a hannuna,fitsararriyar banza da ta hofi,ki b'ace mini da gani ko na karyaki a cikin gidannan na karya banza." Dafe da inda ya mareta tace. "Ni kuma zan nuna maka na isa na karb'arwa Yayarmu hak'k'inta,za ka iya cin nawa kaci bulis,amman banda nata." Tana kawowa nan ta busa masa kararan da ta kwance a leda,da yayo kanta zai daketa,ba shiri ya saki ledar da kud'in ke ciki ya hau susa,yayin da Yusra ta d'auke ledar tana dariya. "Yauwwa Yisra,bani su nan,kinji shale lan jikata" Wani kallo Yusra ta jefeta da shi kafin tace. "Ban tab'a ganin zilamammiyar tsohuwa irinki ba,sai mutum yana da abin duniya yake mutum a gurin ki,ba ga iya jikokinki kad'ai ba,hatta ga 'ya'yanki,kina tunanin da mahaifinmu zai daho yaga irin rik'on da kikayi mana bayan mutuwarsa zai yafe miki?ture wanda kikayi mana da ransa,don sai yafi jin zafin wanda kikayi mana bayan babu ransa,don zaiyi tunanin bayan babu ransa zaki dubemu,sai yaga sab'anin hakan,zan iya rantsuwa duk cikin 'ya'yanki Baba yafi sonki da yi miki biyayya da kuma son faranta miki,amman da Allah ya jarabceshi da babu kika bi kika d'ora masa karan tsana,tunda kika yiwa d'an cikinki su waye mu don kin mana,amman ki tina fa,akwai hisabi tsakanin d'a da mahaifa,domin kiwo ne ya baku,kuma sai ya tambayeku yadda kuka rik'e amanar da ya baku, idan ba ki guji duniya a yanzu da kike neman gangarawa ba sai yaushe,ko mak'iyina ba zan so zuciyarsa ta kasance irin taki ba Iya,wannan kud'in kuwa kinyi kad'an ki ci ko da ficika a ciki,darajar tsufanki ce kawai za ta saka na k'yaleki ban watsa miki kararan nan ba wallahi." Kafin ta juya ta kalli Baffa Shamsu da ke ta faman susa,duk yayi wurgi da kayan jikinsa saura gajeran wando da singileti tace. "Rigima idan ta shafeni mazewa nake,idan aka tab'a Yayarmu kuwa illatarwa nake,zan iya sauka akan ko wani bugire indai akan Yayarmu ne,idan kuma kana ganin k'arya nake ka biyo ni da sunan kazo karb'ar kud'in nan,ko kuma in an kawo lefe wani ya tab'a tsinke a ciki." Tana kawowa nan ta juya ta fita daga d'akin,suka had'a ido da Umma da ke rarraba idanu,ta watsa mata ragowar kararan hannunta,yayin da ta saki ihu ta nufi d'akinta da gudu tana susa don gudun kada tayi tsirara a waje,Baffa Shamsu ma da yaga abin ba na k'are ba ne da gudu ya fice ya nufi gida. "Kawu kayi hak'urin b'oye makan da nayi" Yusra ce ke gayawa Kawu Iliya haka. "Me kika b'oye mun?" Ya tambayeta,yayin da ta kwashe duk abinda ya faru da Nusrat daga barinta gidan Aunty Maryam ta gaya masa inda ta d'ora da. "Yayarmu ce tace kar na gaya maka shiyasa nayi shiru da maganar,gidan k'awata ma da nake ce muku na tafi, gurin Yayarmun nake zuwa,to shine yanzu wanda ya taimaketa zai aureta shine aka kai mata kud'in aure,to sun ce basa buk'atar ko tsinke da za'a kaita da shi,shine Baffa Shamsu ya bata kud'in auran a hannunta,ita kuma tace in kawo maka ka ajiye mata." Idan ta gaya masa yadda akayi ta anso kud'in,zaice ta mayar masa ne don shine k'anin mahaifinsu shi yafi can canta da ya rik'e kud'in a hannunsa,kawai ta yanke gobe insha Allah za taje hisba takai k'arar Baffa Shamsun don a ja masa kunne,ba irin k'anin mahaifin da ake sakarwa komai ba ne,ko Nusrat yanzu ba za ta gaya mata ta anso kud'in ba sai nan gaba,don ta san halinta itama za ta iya cewa a mayar masa ko ya cinye babu komai,itakwa tana jin zuciyarta bugawa ce kawai baza tayi ba idan yaci kud'in nan. Kawu Iliya da Aunty Hafsa sunyi matuk'ar farin ciki da auran Nusrat in,musamman da Kawu Iliya yace ya san Aashiq in da za ta aura mutumin kirki ne,akwai taimakon alumma. 。。。。 A hankali yake sakkowa daga benensa,duk yayi wani iri da shi,yau kusan kwana biyar rabon da ya sanyata cikin idonsa,ya matse kansa sosai,abinci ma in zai sakko yaci sai ya tabbatar sun bar falon,shima kuma yayyagula zaiyi ba kamar daa da yake sakin jiki yaci sosai ba,bai san da kai kud'insa da akayi ba,Hajjaju ce tace kar a gaya masa,har sai an d'aura auran don zai iya basu ciwon kai. Motsi ya juyo a kicin kai tsaye ya nufi can,ya tsaya daga bakin k'ofar yana k'are mata kallo,,tana tsaye tana wanke kwanukan da ta b'ata,tun dosowarsa kicin in taji a jikinta,ga mayen turaransa da ya cika mata hanci,tunda ya tsaya ta daina fahimtar komai,zuciyarta ta tafi garesa gaba d'aya,sai ta koma yin wanke wanken a sanyaye sakamakon da da take yi da kuzarinta,sai da ya gama morewa kallonta kafin ya taka ya shiga cikin kicin in,duk wani taku da zaiyi da bugun zuciyarta yake tafiya,rungumota yayi ta baya yana sauke bakinsa kan kunnanta,a tare suka sauke ajiyar zuciya,wacce ta futo da iska mai d'umi ta sauka cikin kunnanta,rintse idanuwanta tayi tana jin wani abu na tsirgawa ta mararta,a duk sanda sukayi kusanci da Aashiq sai taji irin wannan yanayin,wani zubin ma ko kallonta yayi haka take ji,kuma akansa kawai take karb'ar yanayin. "Duk yadda zan takura zuciyata nayi,amman ta kasa hak'ura da ke,ina so nayi miki adalci cikin rayuwarki,amman sai dai adalcin kokawa yake da numfashina." Yana ajiye maganar yana kuma matseta cikin jikinsa,had'e da sauke mata kiss me matuk'ar d'umi a dokin wuyanta,ji tayi duk gab'ob'in jikinta suna sassarewa,abinda ke tsirgawa ta mararta tana jin fitarsa da d'umi a jikinta,k'afafuwanta sunyi sanyi kamar ba zasu iya d'aukarta ba,tana son magana amman ta kasa saboda yanayin da ke sauka a jikinta,juyo da ita yayi yana k'arewa fuskarta kallo yana shirin sauke bakinsa kan nata ta kautar da fuskarta had'e da dak'unata kafin tace. "Muje na baka abinci tukunna." "Ina jin yunwar,amman nafi buk'atarki akan abincin,domin rashinki ne ya hanani ci,kwatanta rayuwa babu ke Nuss yana sakani ciwon kan da sai na kwana biyu kan ya sakeni,ki daina cewa zaki barni don Allah." Murmushi ta sakar masa wanda ya k'ara jinsa matatce akan k'aunarta. "Aash da Nuss,rayuwar da basa tare ba sunanta rayuwa ba,zan kasance tare da kai a ko da yaushe,har zuwa ranar da numfashina zai tsaya." Tana kawowa nan ta ja hannunsa ta zaunar da shi akan kujerar teburin cin abincin da ke kicin in,kana ta zuba abincin a plate ta soma bashi yana binta da kallo cikin so da k'auna,yana gama ci ta d'auko rubutunsa da ta karb'o gurin Malam ta bashi,itama yanzu kullum sai Malam ya bata rubutu,da hayak'i tana yi,saboda sunyi waya da Asghar ya gaya mishi auran Nusrat in za'ai da Aashiq kuma dama Malam in ya san matsalar Aashiq d'in. 。。。 Saura sati d'aya biki aka kai lefan Nusrat,saitin akwatina shida,Hajja mahaifiyar Asghar Hajjaju ta saka ta had'o lefan,Yusra tana can aka kai lefan ta kafa ta tsare,mutane sai cin cirindon zuwa ganin lefan ake, wasu cewa suke anya kwa ba siyar da ita za'ayi ba,wasu suce ai sunji dama ance wanda zai auretan sau hud'u yana aure matansa na mutuwa a ranar da aka kaisu,k'ila jininsu yake shanyewa yake tsafi da shi,magana dai iri iri babu wacce mutane basa fad'e,inda Umma ta sanu bakin magana tana ta yadawa Yusra magana. "Ki daina dai kirinki tsafi za'ayi da Yayar takun da ki ke girin gid'ishshille a kanta.‘’ "Bak'in ciki ne dai yayiwa mutum yawa,bayan gorin aure da aka gama yi mata,gashinan Allah ya bata miji na kere sa'a,sai dai mutum ya mutu don haushi." Ana gaggama ganin lefan su Khalil suka zo da motocinsu suka kwashesu aka kaisu can gidan Kawu Iliya,yayin da Umma ta dinga fad'in dama dai opay ne mu za'a rainawa hankali, Iya kuwa ina jin dai an saukar mata da,manzon shiriya,tun ranar da Yisra ta gaggaya mata magan ganun nan suke mata ciwo,gami da suya a ranta,ba ta tab'a sanin kuskure take aikatawa ba sai a ranar,ba ta tab'a jin kunyar halinta ba sai a ranar,halintane k'aramar jikarta take fad'in ko mak'iyinta ba za ta so yayi hali irin nata ba,tabbas ta aikata kuskure,kuskuren da babu damar gyara na baya sai dai na gaba,gaban kuwa ta tabbata ba za ta k'ara ko da kwatan shekarun da tayi a baya ba,kuma babu ran Maimuna da Audu bare ta nemi yafiyarsu,uwa uba mijinta Malam,me sonta da k'aunarta,me hak'uri da halayenta,tayi kuka kamar ba gobe,tana neman yafiyar Ubangiji ko za ta samun sauk'in wani abun, gaba d'aya tayi sanyi duniyar ta fita a ranta. "Yisra,don Allah ku yafe mini,kicewa 'Yar baiwa itama ta yafe mini." "Nidai na yafe miki,amman Yayarmu bazan nema miki yafiya gurinta ba har sai na tabbatar da ingancin nadamarki, ba kwad'ayin daular da za ta shiga kike yi ba." Binta kawai tayi da kallo cikin k'unar zuciya,yanzu me son duniya ya haifar mata? 。。。。 "Dan Allah kayi sauri ka fito daga wankan nan,lokaci yana k'urewa fa." "Kaga ni malam kada ka takura mini,kak'i gayan d'aurin auran wa zamuje kuma kazo kana azal zalata." Yakai k'arshen maganar yana fitowa daga toilet in,murmushi Asghar yayi yace. "Kada ka damu,idan munje zaka ji ko na wane,abinda a cikin masallacin estate innan za'a d'aura." Tab'e baki Aashiq yayi yana zama kan stool in mudubi,kyakkyawar fuskarsa ta bayyana a ciki,kafin yasa towel in hannunsa yana tsane ruwan da ke sumarsa. "Dan Allah kayi da jiki,yanzu sai ka tsaya shafe shafe kamar wani mace." Cewar Asghar yana fito masa da shaddar da zai saka daga leda,iri d'aya ce sak da ta jikinsa har d'inkin,shine ya d'inka musu har Aasad,amman da ya karb'a Aasad in dariyar mugunta ya bisu da ita,don yaga Asghar in sai wani zumud'in auran yake,bayan kamar wa'yan can shima haka wannan d'in zai kasance. An d'aura auran,Aashiq Aliyu Gogel,da na amaryarsa Aysha Abdullahi Ahmad (Nusrat)kunnuwansa ba su gama jiyo masa da wacce aka d'aura masa aure ba numfashinsa ya tsaya cak ya zube a gurin, yayin da Aasad yake adduar Allah yasa ya k'arasa can gaba d'aya. Suna d'aki da ita da Yusra sai su Rabeeah,su Baba Azumi suna tare da Hajjaju,da Hajja,sai Mami mahaifiyar Aasad,sai kuma mutanen cikin estate in, ba wani taro akayi ba,don ko su Baffa Ibrahim Hajjaju cewa tayi a rabu da su tukunna a gani,a d'aura aure in komai ya dai daita sai ai shagalin bikin daga baya. Ta sha kwalliyarta cikin shiga ta alfarmaFareeda tana ta zolayarta tayi shiru gabanta sai fad'uwa yake,Ji sukayi ana salati da sallallami a falon ai ta rigasu mik'ewa ta fito karaf a kunnanta maganar ta sauka. "Allah ya amshi ran Aashiq." Maganarsa ce ta jiya da daddare ta fad'o mata a rai. "Nuss,ina jin a jikina na kusa baki fili,filin da zai baki damar auran wani ba tare da tunanin komai ba,in na mutu kiyi murmushi a duk sanda kika tuna ni,idan tunanina yana sakaki kuka to sam kada ki tunanina." Wani irin gunjin kuka ta saki ta zube a gurin. [6/23, 10:50 AM] Rabi: 48 Kai Hajjaju ta rik'e tana jujjuyawa,da na sani yana mugun lullub'eta,daa tasan mutuwa zaiyi da babu abinda zaisa ta matsa sai anyi aurannan,shi kenan yanzu shi da take gani taji sanyi a ranta shima yabi bayansu,dama shi kad'ai ne irinta ya rage mata wanda take gani yake rage nauyin zuciyarta,gashi ya tafi ba tare da ya bar mata wani irin ba,yanzu kam ita babu mutuwar da ba ta ga ni ba,taga ta mahaifanta,mijinta,'ya'yanta,jikokinta,yanzu kawai tata take zaman jiran zuwanta kawai. Nusrat kuwa a gurin da ta zube numfashinta ya dinga sama yana k'asa,rik'eta Yusra tayi tana jijjigata tace. "Yayarmu ki ja numfashin,kada ki sake shi don Allah." Jan numfashin take amman ta kasa jansa daga k'arshe ya tsaya cak,jikinta ya saki gaba d'aya. "Yayarmu" Yusra ta k'walla kiran sunanta cikin fitar hayyaci tana jijjigata,Ramla ce tace. "Ki nutsu Yusra, ba mutuwa tayi ba suma tayi,bari a yayyafa mata ruwa." Farida ce ta mik'o ruwan aka yayyafa mata amman shiru ba ta motsa ba,ganin hakan yasa Baba Hadiza fita harabar gidan ta cewa Kalil ya tayar da mota,kafin ta koma ciki tace su kamota a nufi asibiti da ita,daga Baba Hadizasai Farida,sai Yusra da ta shige gaban motar suka tafi asibitin,suna zuwa aka karb'eta don bata taimakon gaggawa,musamman ma da aka ga daga gidan da suke. "Dogon suma tayi,zata farka insha Allah." "Ai ba son farkawar tata nake ba,saboda itama tsafi ya nuna bazaiyi aiki a jikinta ba,kamar yadda baiyi a jikin Falisha ba,shiyasa na saka aka fasa cewar Aashiq ya mutu,don estate in ta hargitse mu samu damar kashe Nusrat in, amman maganar gaskiya ban sani ba yana raye ko ya mutu,sai dai na san suna tare da Asghar ban kuma san a ina ba,na kira shi shima tsinanne yak'i d'agawa,in bai wasa ba zai riga Aashiq in yin gaba wallahi,to kuma sai gashi tazo hannu cikin sauki don haka so nake ka k'arasata da wannan allurar." "In dai aikinka ne ban jin yinsa saboda na san zaka min biya da me kauri,bara na d'auko sirinji." "Ok" Yace da shi yana peaking in wayar da ta shigo masa,had'e da nufar k'ofa zai fita,sauke nunfashin da ta rik'e tun d'azu tayi,saboda kada su san ta farka,kafin tayi saurin sakkowa daga gadon ta nufi k'ofar za ta fita,gabanta na dukan tara tara,sai dai tana kai hannu za ta tab'a handle in k'ofar taga alamun ana murd'asa ta waje,sai tayi saurin b'uya a bayan k'ofar,Aasad yana shigowa da yake kansa yana kan waya bai lura da babu kowa akan gadon ba,sai da ta bud'e k'ofar ta fice da gudu,kana ya d'ago ya kalli gadon yaga wayam,bai san sanda yayi wani irin zagi ba ya biyo bayanta,da gudu ta iske Baba Hadiza da Farida. "Ku tashi mu gudu mu bar asibitin nan,ku tashi." Shine abinda tace da su,ba ta saurari me zasu ce ba tayi hanyar da za ta sadata da waje da gudun gaske,su Baba Hadiza suka bi bayanta a tsorace,suna tunanin ko ta haukace ne,Fareeda tana yi tana waigawa ko za ta hango Yusra,kada ta dawo ta tarar ba sa nan. "Ba wata matsala ba ce insha Allah,ya shiga rud'u ne,amman zai farka insha Allah ba da jimawa ba" Cewar Dr Sa'ad yana kallon Asghar,jinjina masa kai kawai Asghar yayi,kafin Dr Sa'ad in yayi mishi sallama ya tafi,bai jima da tafiya ba Aashiq in ya farka,idonsa akan Asghar ya fara sauka,a hankali ya mik'e zaune yana jin yadda kansa yayi masa matuk'ar nauyi. "Rayuwar wa kuka saka cikin had'ari?" Ya jefowa Asghar tambaya."Ba mu saka rayuwar kowa a had'ari ba,ka kwantar da hankalinka insha Allahu wannan karan babu abinda zai samu auranka." "Ba zaka gane yanayin da nake ciki ba Asghar" Yace haka,muryarsa na bayyanar da yadda zuciyarsa tayi rauni,Nusrat kawai yake son gani ya shiga jikinta ko zai samu nutsuwa. "Kira mini Nuss" "Ita da take amarya ai ba zaka samu damar ganinta ba,ka bari zuwa dare tukunna." Wani irin bugawa zuciyarsa tayi har sai da ya danneta da hannunsa kafin yace. "Idan Nunus ta bar rayuwata bazan tab'a yafewa kaina ba,nima kuma na tabbata bazan k'ara ko minti aya a duniya ba zanbi bayanta." "Ba za ta mutu ba,ka daina kawo hakan a ranka." "Ta ya kake son na yadda da kai,Falisha sai da na saki jiki sannan ta barni,Nunus kuwa zuciyata ce ita da rayuwata gaba d'aya,rashinta yana nufin rasani nima." "Tabbas za ta mutu,amman ba yanzu ba insha Allah,za kuyi rayuwa mai tsayi da izinin Allah,za kuma kace na gaya maka." "Ka kira mini ita don Allah" Baice komai ba ya d'auki wayar Aashiq in da ke gefensa ya lalubo number in Nusrat in ya danna mata kira,sai dai har yayi 4miss call ba tare da an d'aga ba. "Kira Yusra" Aashiq yace da shi don yasan duk inda take to tabbas suna tare,bugu d'aya yayiwa number in Yusran ta shiga,a lokacin suna tsaye suna jiran tsammani daga likitan da ya shiga gurin Nusrat in wayar ta shigo mata,hannunta na rawa ta d'aga saboda ganin me kiran,Yayanmu,kamar yadda tayi saving in numbersa,da ta d'aga kwata kwata ba ta jin me ake cewa, hakan yasa tayi d'an gaba da gurin da suke,tana tunanin ko gurinne babu network, wata kujera ta samu ta zauna akai,tana shirin bin bayan kiran sai gashi wani ya kuma shigowa da hanzari tayi peaking. "An tayar mana da hankalin cewa ka mutu,gashinan Yayarmu ta suma,har yau an kasa gano kanta." Ta kai k'arshen maganar hawaye masu zafi na biyo kuncinta." "Subhanallahi yanzu tana ina Nusrat d'in?" Jin muryar Asghar ba ta Aashiq ba ta sa ta cewar. "Yaa Asghar ina Yayan namu,ko ya mutun da gaske ne?muna nan asibitin gogel." "Go me?" Ya tamvayeta a gigice."Gogel" Ta bashi amsa,d'if ya kashe wayar,bai tsaya ya saurari Aashiq ba ya zari key in mota ya fice a gagauce,yana zuwa bakin gate in Nusrat na fitowa da gudun gaske,Allah yasa idonsa ya sauka a kanta,"Nusrat" Ya k'wala mata kira yana zaune a cikin motar,tana waigowa kwa idonta ya sauka a kansa ta nufi motar,su Farida ma da suka fito suka maro mata baya,gaban motar ta bud'e ta shiga ta zauna,sai a sannan wani azababban kuka ya kubfce mata,baice da ita komai ba ya barta ta samu nutsuwa tukunna,ko su Baba Hadizan bai tambaya ba da suka bud'e gidan baya suka shiga,yana k'ok'arin tayar da motar Farida tace."Yusra kar tazo tana nemanmu ban san inda tayi ba." A firgice Nusrat ta d'ago jajayen idanuwanta. "Bari na kirata a waya tazo ta samemu mu tafi." Cewar Asghar yana nemo numberta ya danna mata kira. Gaba d'ayansa ya shiga tashin hankali mara misaltuwa,ya rasa wani irin tunani zaiyi,shikenan asirinsu ya gama tonuwa, bashi da wani abu da zai kare kansa dole sai an tuhumesa,tuhumar da za ta tono abubuwa da dama,kawai ganin Yusra yayi a gabansa tana tambayarsa. "Banga su Aunty Frida ba,ko Yayar tamun ta farfad'o ne?" Hannunta ya ja zuwa d'akin ba tare da yace mata komai ba. "Idan kina son rayuwarki da ta Yayarki ta tsira,to ki kira wayar da za ta had'ani da ita yanzun nan." Zaro idanuwanta tayi don ba ta gama fuskantar inda maganarsa ta dosa ba,sai kuma ga kira ya shigo wayarta,fusge wayar yayi yana k'arewa number kallo,tun a kallo d'aya da yayi mata yasan number Aashiq ce. " Yaa Asghar ne." Baice da ita komai ba yayi peaking wayar yana sakata a speaker kafin ya d'ora mata wuk'a a mak'oshinta. "Yusra kina ina ne?Ki fito muna bakin gate muna jiranki." Muryar Asghar ta bayyana a cikin wayar. "Ina Yayarmun?" "Ga ta nan muna tare." "Bata wayar" "Ok tom" Yace yana bawa Nusrat wayar, ba ta kai ga magana ba taji muryar Aasad. "Idan kina son rayuwar k'anwarki zaki iya jan bakinki kiyi shiru da abinda kika ji,muddun kwa kika gayawa ko mutum d'aya ne,to da ke da shi da k'anwarki zaku bak'unci lahira a yau yau d'in nan." Rintse idanuwanta tayi hawayen tashin hankali na kuma zirarowa ta kuncinta. "Me tace?" "Tace tayi nisa za ta biyo keke nape ya ajiyeta." "OK" Yace had'e da tayar da motar suka nufi gida." Aasad kuwa bayan ya kashe wayar,rotsata yayi da k'asa,wayarta sabuwa fil Aashiq ne ya siyo mata ita, anan ya bar wayar ya shek'awa Yusra wani abu,kafin ya d'auketa subi ta k'ofar baya, dama ta nan ya biyo ya ajiye motarsa,don haka ya sakata a ciki yaja ya nufi gidansa da ita,yana jinsa cikin nutsuwa, zai saka a rufe bakin Nusrat da k'anwar tata ne,kafin ya saketa,in yaso kawai Aashiq zai masa allurar da zata mayar da rayuwarsa tamkar ta yara,daga nan dole yasan zai saki Nusrat shi kuma sai ya aureta,dama har yanzu zuciyarsa tana nunfasa mata,kawai dai don yafi son DUNIYA da ita ne... [6/24, 10:35 AM] Rabi: 49 Baba Hadiza da Farida kawai ya sauke a gidan Hajjaju,ya wuce da Nusrat gidansa,acan ne yakai Aashiq,bayan ya sume a gurin d'aurin auran,har lokacin Nusrat kuka take,tak'i bashi damar ma da zai tambayeta abinda ya faru,a falo ya tsaya ya nuna mata bedroom in da Aashiq in ke ciki, duk ma ko meye idan taje ta gaya masa,ba tayi tunanin ko Aashiq inne a ciki ba,ita dai ta bud'e k'ofar kawai ne ta shiga,don dama tana buk'atar kad'aici don yin tunani kan matsalar da ta kunno kai,rayuwarsu ita da Yusra ko kuma dai daituwar rayuwar Aashiq?Ba ta san wanne za ta zab'a ba,tana bud'e k'ofar ta mayar ta rufe,ta jingina da ita tana lumshe idanuwanta wasu sababbun hawaye masu zafi suka kuma biyo kuncinta,k'arar bud'e k'ofar da ta ji yasata bud'e kumburarrun idanuwanta da sukayi jajir a saitin gurin da taji k'arar,Aashiq ne ya bud'e k'ofar toilet ya fito,wanka yayi had'e da d'auro alwalar sallar azahar,a cikin idanuwanta nasa ya sauka,sai da yafara mayar da su ya lumshe kafin ya kuma bud'esu a kanta ,hannuwansa ya wara mata,alamun ta taho gareshi koma meye zaiji zai kuma yi rarrashin,kamar dama so take ta jita a jikinsa zuciyarta ta kuma karyewa,ta fashe da wani matsanancin kukan,tsam tsam ya shigar da ita jikinsa,yana shafa bayanta alamun rarrashi amman kamar k'ara zigata yake,da ita a jikinsa ya nufi toilet,ya isa gaban shower had'e da kunnata,jin saukar ruwan yasata yin shiru tana kuma shigewa jikinsa, yayin da shi kuma yake lalubar zip in rigarta,yana jinsa ya jashi k'asa,da yake gown ce a jikinta ta farin leshi sai ya fara k'ok'arin zame mata ita,ganin hakan da tayi yasata k'ara k'ank'amesa sosai,amman da yake k'arfin ba d'aya ba sai da ya d'agota ya zame rigar tayi k'asa gaba d'aya, ba ta bashi damar k'are mata kallo ba tayi saurin shigewa jikinsa,duk son d'agotan da yake tak'i bashi damar hakan, a haka yasa hannunsa ya b'alle fara k'al in breziyar da ke jikinta,ya zare hannuwan,kuma k'ank'amesa tayi,don ba ta son ya d'agota ta kalleta a hakan,had'uwar k'irjinta da nasa da babu riga sai da yayi kokawa da numfashinsa,kafin ya saukeshi a hankali yana kuma matseta sosai yanayinsa yana kuma sauyawa,hannu yasa yana zame undies had'e da pant in jikinta suma farare da su k'al,sai dai suna zamowa k'asa idonsa ya sauka akai sun d'an b'aci da jini,bakinsa ya saka dai dai kunnanta yace. "Me yasa bak'wanki bai tashi zuwa ba sai yau da nake da damar kasancewa da ke?" Bai jira me zata ce ba,don yasan ba zata ce d'in ba ya kuma rik'eta tsam yana jin kamar kar ya rabata da jikinsa,sai dai dole ne ya fita ya barta ta kimtsa kanta,don yaga alamun kunyarsa ba za ta barta sakewa ba,sai kuma shigewa jikinsa take,kuma ya san don kada yaga k'irjinta ne,ba ta san hakan da take kuma kunce saitin kansa take ba,a hankali ya fara rabata da jikinsa,ita kuma tak'i yadda da hakan. "Zan fita na barki ki gyara ne,in kuma na gyara ki to?" Zamewa tayi daga jikinsa tana yin k'asa ta had'e guri d'aya cikin matsananciyar kunyarsa,kallon yadda fatarta take wani d'aukan ido yake,ruwan da yake sauka jikinta yana zirarewa saboda santsinta,kafin ya juya ya bar mata toilet in cikin yanayi na buk'atuwa,yana fita ta kashe shower in,kafin ta fara wanke undis da pant in daga bisani ta had'a da breziyar ma ta wankesu ta shanya a band'akin,ta yo wanka ta d'auro tawul mai d'an girma,ta d'aura wani a kanta da ya jik'e jagab,kafin ta fito toilet in,tana jin yadda sanyi yake shiga cikin k'asu suwanta, Aashiq kuwa toilet in falo ya shiga ya sakarwa kansa shower sai da ya d'an samu nutsuwa kana ya sake yo wani wankan had'e da d'auro alwala ya fito,idonsa ne ya sauka kan wayarsa da Asghar ya ajiye kan TVstand,dama yana da buk'atarta,don haka ya d'auka yayi musu online shoping,kafin ya shiga bedroom in da ya san na Asghar ne,ya duba wadrobe d'insa ya d'auki jallabiyarsa ya fito,ya tayar da sallah anan falon,bai jima da idarwa ba yaji nocking yasan kayansu ne suka iso,su d'inne kuwa ya anso kana ya nufo bedroom in da Nusrat ke ciki,tana gefen gado a zaune tana ta rawar d'ari,don sosai sanyin yake kuma shigarta,yana ganin haka ya d'au remort in Ac ya kashe, da kansa ya d'auko pant cikin siyayyar da aka yo musu,ya manna mata audiga a jiki,duk da ba tab'a yi yayi ba amman yana gani ya fuskanci abinda yake nufi,mik'ar da ita yayi tsaye ya saka mata pant d'in da undis kafin ya rik'ota zuwa gaban mirro ya zaunar da ita kan stool,ya cire tawul in da ta d'aura a kanta, handrayer ya jona ya fara busar mata da kanta, yana gamawa ya had'e mata shi a k'eya yadda bazai dameta ba, kafin ya d'auko doguwar riga ya saka mata,saboda bata da wani k'arfi,zazzab'in ya kuma rufeta ruf, da k'yar take bud'e idanuwanta da suke a kumbure sunyi jajir saboda kukan da tayi, akan gado ya kwantar da ita ya lullub'a mata bargo mai d'umi kafin ya fara kiran number Dr Sa'ad. Kafin zuwan Dr Sa'ad jikin nata ya kuma rincab'ewa sai wani irin surutai take,cikin surutan nata Yusra kawai yake fahimta,har yayi tunanin kiran wayar Yusran sai dai yajita a kashe,allurar da zata saukar mata da zazzab'i da kuma ta bacci Dr Sa'ad yayi mata,kana yace zai aiko masa da magun gunan da in ta tashi za'a bata, insha Allah za ta samu sauk'i,kafin ya mishi sallama ya tafi,shi kuma ya d'auketa suka koma bedroom d'in,ya kwantar da ita ya rufeta da bargo, mintina kad'an sai ya duba kai kawon nunfashinta yana tsoro sosai yana tsoron ta tafi ta barshi don bai san hakan me zata haifar ba. "Idan nace maka Nusrat 'yata ce ta cikina zaka yadda?" cewar Baba me amsa sunan Malam a gurinsu yace da Asghar. "Zan yadda mana,saboda akwai kama ta jini a tare da ku,kuma ta tab'a gayan tana jin kusanci da kai sosai, banda mahaifinta ya rasu za ta iya cewa kai d'in mahaifinta ne,tun daga nan na fara tunanin akwai alak'a tsakaninku sai dai na bari ka sanar mini da kanka." "Mutum a fuska baka sanin zuciyarsa Asghar,wannan dalilin ne yasa nayi shiru da bakina, na bari sai zuciyata ta nutsu da kai, nayi matuk'ar mamakin ganin Nusrat cikin estate d'in nan,sai dai babu halin yi mata magana idan ina son mu tsira cikin estate d'in nan, yanzu dai kafin kaji komai ina so kaxo min da ita." Sai dai Asghar yana zuwa ya tarar da Nusrat d'in babu lafiya,don haka ya koma ya gayawa Malam d'in yace su barwa gobe idan Allah ya bata lafiya... [6/26, 12:11 AM] Rabi: 50 Aashiq gadin Nusrat ya zauna yi,mintina kad'an ya lek'a k'irjinta ya tabbatar da tana numfashi,sallah ce kawai ke tashinsa,yana idarwa zai dawo gefenta ya zauna,sai da akayi sallar isha kana ya tashi zuwa kicin ya dafo black tea insa na k'aida ya dawo d'akin ya zauna yana sha, mutsu mutsu yaga Nusrat tana yi sai ya ajiye tea in akan drowar gado ya haura kan gadon yana janye bargon dake jikinta,gumi yaga tana had'awa sosai alamun zazzab'in ya sauka,remort d'in Ac ya d'auka ya k'ure k'arfinta,a firgice ta farka tana wani irin kuka tana kiran sunan Yusra,jijjigata yayi yana kiran sunanta,amman tak'i sauraransa idonta a rintse yake tana kiran sunan Yusra,ganin yayi yayi ta saurareshi tak'i yasa ya d'auki wayarsa ya kira wayar Yusran kusan sau hud'u tak'i shiga, sai ya kira Khalil yace yaje can gidan Hajjaju ya taho masa da Yusra,kafin yaci gaba da rarrashinta,ya samu tayi shiru cikin jikinsa tana ta sauke ajiyar zuciya. Khalil da yaje neman Yusra aka sanar masa ba ta nan,har Farida na cewa tayi tunanin ma Yusran ta dawo suna tare da Nusrat d'in,jin hakan da Khalil yayi sai ya kira wayar Aashiq ya gaya masa,shi kuma sai yace yaje can gidan Kawu Iliya ya dubo,can ma dai da yaje Aunty Hafsa ta sanar masa Yusran tana nan estate d'in,da ya kira Aashiq ya gaya masa sai lamarin ya d'aure masa kai ainun,to ko dai wani abu ne ya samu Yusran shi yasa Nisrat d'in take irin wannan kukan?Gashi bacci ya kuma d'aukar Nusrat d'in bare ya tambayeta,sai ya kira wayar Asghar yake tambayarsa abinda ya faru,sai Asghar yace ya fito falo suyi maganar da yake shigowarsu cikin gidan kenan shi da Ramla,sai Ramlan ta shige bedroom inta d'auke da 'yan biyu ta bar Asghar d'in yana jiran fitowar Aashiq. "Nayi tunanin ko ta gaya maka abinda ya faru,don a gigice naga ta fito daga asibitin,wanda nima tunanina wani abin zai iya samunta a asibitin,shiyasa Yusra tana gayan suna can na tafi d'aukosu." "Ba ta gaya mini komai ba,banda sunan Yusra babu abinda take fad'i,kuma na kira wayar Yusran ba ta shiga,na saka aje a taho da ita,duk inda ake tunanin samunta ba ta nan,dama ba tare kuka dawo ba?" "Babu ita suka fito daga asibitin,da na kira wayarta kuma sai tace na bawa Nusrat,to bansan me ta cewa Nusrat d'in ba,amman naga takuma firgicewa,da na tambayeta sai cewa tayi,Yusran tace muje ta taho." "Mtssss,Asghar jikina yana bani akwai matsala." "Ni kaina ina jin hakan,hankalina bai kwanta da wayar da sukayi da Yusra ba,amman kamar wayarka tana nad'ar sautin magana ko?" "Anyi haka,bara na d'auko a duba." Ya nufi bedroom in ya d'auko ya kawo masa shi kuma ya shiga bin binkitawa,ya shiga wannan yaji ba maganar bace ya shiga wannan a haka har suka samu abinda suke so, muryar Aasad rangad'a d'au ta fito da abinda yacewa Nusrat. "Biri yayi kama da mutum,ina zarginsa sosai a kanka,tunda na tab'a jinsa yana waya akan a kashe Malam,nasan akwai wata munak'isa da yake shirya maka,abinda ya dakatar da ni a kansa,saboda Malam bai gaya mini dalilin da yasa suke neman kasheshi ba,kai kuma ban san ta ina zan fuskantar dakai ka fuskanta ba,abin tashin hankalin kuma ba mu san me Nusrat d'in taji ba,ga kuma Yusra da rayuwarta ke cikin had'ari." Dukkaninsu shiru sukayi ko wanne da tunanin da yake sak'awa a ransa,kafin Asghar ya tashi ya fita daga cikin gidan,bai jin ko ya bud'e bakinsa zai iya yin magana a halin da yake jin zuciyarsa,yana kallo Asghar d'in ya fice ba tare da ko tambayarsa inda zashi yayi ba. Ya kwana da sanin tun bayan mutuwar Alisha Aasad baya kwana cikin estate d'in nan,bai damu da sanin inda yake kwana ba saboda yasan yana sharholiyarsa da 'yan mata,kuma ba wani shiri suka cika yi ba yawancin had'uwarsu da fad'a suke rabuwa,saboda kowa ya gano inda yasa gaba akan Aashiq, ya tabbata duk inda Aasad yake a yanzu can yakai Yusra,don haka ya saka akayi tracking numbersa,ya d'ebi 'yan sanda suka nufi can,me gadin gidan nasa suka saka yayi nocking,da yaji muryar me gadin bayan ya tambayi waye sai ya bud'e kai tsaye don a tunaninsa ko wani abu ne ya faru me gadin yazo sanar masa,daga shi sai gajeran wando ya fito,ganin 'yan sanda suna nuna shi da bindiga sai yasha jinin jikinsa amman ya maze yace."Lafiya?" "Lafiyarce ta kawomu." Cewar Asghar yana fitowa daga bayan 'yan sandan da ya tsaya,kafin ya basu umarnin su kama shi."Me nayi?" Ya fara fad'e yana fus fusgewa,Asghar da wani d'an sandan suka sa kansu cikin gidan,dai dai fitowar Baby daga ita sai tawul,taji Asghar d'in shiru shine ta biyo bayansa,tana ganin d'an sanda ta arci na kare ta koma had'e da datso k'ofa,d'aki d'aki suka duba a d'akin k'arshe suka sameta,marabarta da gawa numfashinta da ke kai kawo a k'irjinta,don har lokacin abinda ya shak'a mata bai saketa ba,Asghar ne ya d'aukota yana k'arewa innocent face inta kallo,jallabiya d'an sandan ya gani kan kujera ya d'aukowa Aasad suka fito,aka bashi ya saka rigar,yana sakawa yana kallon Asghar yana k'wafa. "Wallahi sai kayi da na sani,domin kama ni yana nufin tono abubuwa da dama tonowar da baza tayi maka dad'i ba,zaka ga abinda zatonka bai tab'a baka ba,kuma na tabbata hakan sai yafi tab'aka sama da kowa." Asghar bai kulashi ba,don ya d'au maganarsa a zafin tonuwar asirinsa da bai tab'a zata ba. Dr Sa'ad ya kira ya duba Yusra ya tabbatar da lafiyarta k'alau,abinda ya shek'a mata ne yafi k'arfin jininta zai saketa insha Allah nan da safiya,Nusrat ta farka a lokacin sai taji ta samu nutsuwar zuciya,tasan ba kowa ne da wannan aikin ba sai Asghar,yayin da ta shiga yi masa godiya domin rayuwarta ya ceta ba ta Yusra ba,daga Asghar har Aashiq d'in babu wanda ya mata tambayar abinda taji,shi Aashiq bai shiryawa ji ba yayin da Asghar ya barwa zuwa safiya. Wanka tayi ta gyara jikinta,sai a lokacin taji wata mitsiyaciyar yunwa,Aashiq ba ya d'akin yana can falo tare da Asghar da ya saka Ramla sama musu sassauk'an abinci don daga shi har Aashiq d'in baijin akwai wanda ya d'orawa harshensa wani abu a wunin yau,wanda ya tabbata kwana a hakan zai basu matsala,shirya kanta tayi cikin doguwar rigar baccin da iya kacinta guiwarta,sai dai ba me nuna tsiraici bace shiyasa ta daure ta sakata saboda rashin abinda za ta saka d'in,bud'e k'ofar tayi ta lek'o sai ta hango su tare da Asghar sai ta koma,don baza ta iya fita a haka ba,ko shi kad'ai d'in za taji nauyin ya ganta a haka,sai dai kawai don ba yadda za tayi,d'an buga k'ofar tayi,yana jin haka ya taso ya nufo bedroom d'in. "Yunwa" Ta fad'a tana dak'una fuska idonta cikin nasa,lumshe idanuwansa yayi ya kuma bud'esu a kanta,kafin ya juya ya fita,hijabi ya anso mata gun Ramla har k'asa,ta saka ta fito,yace taje kicin ta taya Ramlan,don zai so cin wani abu da ya fito daga hannunta. Ta murzu sosai a gurinsa don ya kasa hak'uri sai da ya rage zafi da ita,a tunaninsa idan ya jita cikin jikinsa zai iya samun bacci amman ina,yadda take manna k'irjinta a nasa tana mimmik'ewa duk a cikin bacci yafi komai kunnashi,kunnawar da babu abin kashewa,don haka ya hanata baccin sai da ya rage zafi tukunna suka samu sukai bacci, ko ina na jikinta yana rad'ad'i musamman lab'b'anta da k'irjinta,don baiyi musu rik'o na wasa ba,sun murzu iya murzuwa,musamman yadda dama tsakaninsa da su kallo ne ya dad'e yana kwatanta yadda laushi da santsinsu zai kasance a hannusa,bai tab'a tunanin hannunsa zai sauka a kai ba don bai gano yuyuwar aure tsakaninsu ba. Zuwa safiya Baffa k'arami ya samu labarin kama Aasad,inda yake ta banbami da bala'i,sai dai kuma yaje har police station d'in sun k'i saurararsa,amman sun gaya masa wanda uasa su kama shi,inda yazo ya samu Baffa ya gaya masa,shi kuma ya dinga kiran wayar Asghar sai dai tak'i tafiya gaba d'aya. Nan gidansa Asghar ya d'auko Malam ya kawosa,a gaban Nusrat da Yusra da ta tashi k'alau da ita babu ciwon komai a jikinta ya cire k'asimbar da ya saka da suma,a kusan tare suka furta. "Babaa" Jinjina musu kai yayi,yayin da suka tsaya kallon kallo tsakaninsu. " 'Yar baiwa nine,mahaifinku ne ni,ban mutu ba,k'arya likitan nan yayi muku sun so dai kasheni,kinga wanda ya cece ni nan." Yakai k'arshen maganar yana nuna Asghar. "Dama kai suka so yiwa allurar mutuwa kenan,kamar yadda nayi zato?" Jinjina mata kai yayi,wasu hawaye ne suka biyo kuncinta sai dai hawayen farin cikin kasancewar mahaifinta a raye bai mutu ba. "Tunda na ganka nake jin kusanci tare da kai,har Yusra na gayawa tace mun tunda ka mutu me zai dawo da kai? Me yasa ka b'oye mana kanka Baba?" "Saboda tsira da rayuwata da taku,sun riga sun san ina raye,kuma ba su hak'ura da neman inda nake ba,sai dai ba su san cewa ina cikin estate d'insu ba,Asghar ne ya taimake ni,ya b'oyeni a cikin gidan nan ba tare da sanin kowa ba,har zuwa sanda ya fuskanci ni d'in malami ne,shine ya rok'i in dinga yiwa d'an uwansa rubutu,ya gaya mini halin da yake ciki, yanzu ba lokacin tambayar me ya kawoki nan bace, camerar da nace ki d'auke mini zaki bani,domin akanta ce suke neman rayuwata." Shiru Nusrat tayi,tunda yace ta d'auko camerar ta ajiye zai dawo,ba ta tab'a bud'e wa ba,ta dai k'ulle a leda ta saka cikin kayanta,tana yawan d'auka ta kalla ta ajiye,wani b'ari na zuciyarta yana gaya mata kamar yadda yace zai dawo,ashee zai dawo d'in,shirunta yasa gaban Babaa da Asghar fad'uwa,don sun tattauna akan camerar,kuma itace hujjar da suke da ita wacce zata tona asirin Aasad da masu goya masa baya. ,"Tana nan na ajiye kamar yadda ka umarce ni,sai dai Baba wanda yaso akasheka shi yaso a kasheni nima,ya kuma sace Yusra,saboda suna neman ruguza rayuwar Aashiq,matan da duk yake aurq suna mutuwa sune suke kashesu." "Ban fahimci komai ba,don Allah ku fahimtar da ni." Cewar Aashiq yana kallonsu,Asghae yace. "Zaka fahimta ne a yau d'in nan,duk wani me neman durk'usar da rayuwarka zamu ganshi za'ayi walk'iya kowa ya gani." Sanarwar taro akayi a cikin estate d'in,duk wani me rai da motsi da yake ciki ana buk'atar zuwansa, sai kuma ga zuwan Baffa Ibrahim da mahaifansa,kakannin Aashiq na gurin uwa kenan,da mahaifan[6/27, 10:55 PM] Rabi: 51 Ko kad'an tunanin Baffa da Baffa k'arami,bai basu cewar asirinsu ne ya tonu ba,don haka zuciyarsu d'aya suka nufi gurin taron,Aasad ma 'yan sanda sunzo da shi gurin,yayin da Asghar ya fara bayanin dalilin had'a taron, akan masu kisan matan Aashiq ne da yake aura suna mutuwa,insha Allahu a yau Allah zai tonu asirinsua k'atuwar TV aka saka vidion kisan Falisha,iya gurin kisan nata suka kunna don wancan yayi muni da yawa. Baffa ne ya tashi yace."To ai cikin wanda sukayi kisan babu fuskar ko d'aya daga cikin estate d'in. "Na sani Baffa babu fuskar kowa a cikin nan da muke zaune amman na tabbata akwai fuskar wa'yanda suka saka su." Baffa k 'arami ya kasa katab'us gumi sai mugun keto masa yake,musamman idan ya d'aga ido ya kalli fuskar Aasad da ke k'ulle da sark'a,shirin fad'ar gaskiya yake,yadda ta kwab'e mishi ta kwab'ewa kowa ma,Baffa kuwa banbami ya shiga yi ya hau Asghar da fad'a."Ni ba na son rashin hankali banda hauka da shiri rita ina kake da hujja,har da zaka zo ka tara mu a nan,shi Aasad in da ka saka aka kama ubanka yayi maka,na gaya ma tun wuri ka saka masu bak'ak'en kunnuwan can su sake shi,mutuwar matan Aashiq kuwa mun barwa Allah,wannan videon zai iya yuyuwa ma ba na gaske ba ne,don haka kowa ya watse daga shirmen taron nan,idan ka kuma d'aga maganar nan sai na tsine maka wallahi." "Babu inda za'a je domin ni nan nine hujjarsa." "Kai kuma dalla can daga ina,security kuzo ku fice mana da wannan mahaukacin." "Bashir" Baffa Ibrahim ya kira sunansa. "Borin kunyar da ka fara tun yanzu ya isa, ni kaina akan maganar nazo,da kuka rufe mini baki yau Allah ya bud'e mini shi, bawan Allah muna jinka wata hujja ce da kai?" Yakai k'arshen maganar yana kallon Baba,yayin da Baba ya shiga koro musu bayanin duk abinda ya faru,tun daga kan yadda camrra tazo hannunsa,ya kuma d'ora da Aasad shine shugabansu,yasan komai da ke faruwa harma da wanda suke samansa,yayin da Aasad yaga bashi da wata mafita illa ta ya fito da gaskiyar abinda ya sani don bazai bari ta kwab'e mishi shi kad'ai ba,shine ya shiga bayyana musu duk abinda ya faru,ya kuma d'ora da Baffansa da Baffan Asghar su suka saka aka kashe Baffan Aashiq,sannan su sukayi tsafin da duk matan da yake aura suke mutuwa,Falisha ce tsafi ya nuna bazaiyi aiki a kanta ba,Alisha kuma taji yana waya ne za'a kashe Falisha,shine garin tazo ta gayawa Aashiq tayi hatsari ta mutu,kuma Maminsa ita ta sakawa Ammin Aashiq guba a abinci taci ta mutu,da jin wannan batu tuwa jikin kowa ya mutu,mamaki gaba d'aya yabi ya kashesu,yayin da Baffa da Baffa K'arami jikinsu yake ta mugun rawa suna rarraba idanu,ita kuwa Mami a zaunen da take gudawa take ta fesarwa,Asghar kuwa tunda yaji bayyanar sunan mahaifinsa cikin abinda bai tab'a hasasho hakan,kuma gashi ya kasa musawa ya kasa k'aryata hakan,daga ganin yadda take muzuru sun aikata d'in,abinda Aasad yake yawan gaya masa kenan,baiyi k'arya ba don kwa yaga abinda zatonsa bai tab'a zata ba,kuma hakan ya tab'ashi sosai,yayin da 'yan sanda suka kad'a kawunansu zubewa yayi a gurin,haka ma Hajja wani irin kuka take,ba ta tab'a tunanin mijinta zai iya aikata hakan ba,ko a fuska ba ta tab'a ganin ya nuna yana k'in Aashiq ba,sai ma nunawa yake kamar yafi sonsa akan Asghar,ashe duk makirci ne,k'annen Aasad suna gani police suka tisa k'eyar Mahaifinsu,mahaifiyarsu,yayansu,wani irin kuka suke na kaico da halin nasu,basu so suka zo a haka ba,ga Kakanninsu sai tsinewa Baffan nasu suke,suna wadaran da haihuwar irinsa,har Mami da Aasad d'inma ba su bari a baya ba suna ta jifansu da mugayen kalamai,ko wani suka gani ya cutar da Aliyu ba su san hukuncin da zasu iya yi mishi ba, sai gashi d'an cikinsu ne ya aikata hakan saboda CIN AMANA,duk abinda yayi masa yayi musu bai gani ba,burinsa dukiyar da ba guminsa ba ta dawo hannunsa, ko wani ne ya bawa Hajjaju labarin Bashir da Hamza zasu aikatawa Aliyunta haka,tabbas za ta k'aryata da gasken gasken duba da aminci da soyayyar da ke tsakaninsu tun k'uruciya shi da Hamza,Bashir kuwa darajar mahaifinsa wanda yake wan Hajjajun Aliyun ya duba ya janyosa jikinsa,da kuma jininsu da ya zamto d'aya daace mahaifin Bashir d'in zai dawo yaga abinda d'ansa ya yiwa d'anta ta tabbata sai yayi wadaran da haihuwarsa,mahaifiyarsa da 'yan uwansa ma in suka ji zancan duk sai sunyi Allah wadarai da shi,Aashiq kuwa ya rasa me yake masa dad'i cikin duniyar kawai yana zaune ne gashinan,bai tab'a tunani ko hasashen akwai saka hannun wani cikin lamarin rayuwarsa ba,yanzu ko wani laifi yayi musu ya can canci cusgunawa da musgunawa rayuwarsa da suka yi,bayan sunyi silar zamtowarsa maraya tun daga k'uruciyarsa,suka hanashi karatu,suka kuma hanashi aure,saboda kar ya samu nutsuwq da jin dad'in rayuwa,duk da kasancewarsa mabuk'aci da bai rik'e kansa ba da yanzu yayi k'aurin suna gurin aikata zina,duk da sunyi amfani da damuwa da k'uncin zuciyar da yake ciki,ya karb'i tayin shan giya da cocaine d'in da sukayi masa,yanzu meye ribarsu,wani dad'i suka ji da zamtowarsa hakan?dukkaninsu bai tab'a ganin ko alamun tsana ko d'igo daga garesu ba,sai ma soyayya da kowa yake k'ok'arin nuna masa ashe nan duk gaibu ce. Baba sam bai ji dad'in abinda mahaifiyarsa da 'yan uwansa suka yiwa Nusrat ba,da ba don Allah ya jefota hannu na gari ba da shikenan sunyi silar gurb'acewar rayuwarta ko kuma ma a rasa wacce duniyar ta shiga,sun mata abinda shi bazai tab'a yiwa jininsu ba ko da kwa a yanzun ne,ko da kuma cikin shegen tayi da gaske. Khalil ne ya d'aukko su,bayan Nusrar ta sanarwa da Hajjaju zasu je can gidansu da Baba,shine Hajjajun tace tayi zamanta acan bayan lafawar komai za'ayi shagalin biki,sai azo a d'auketa,Aashiq kuwa tex ta tura masa ta waya,don rabon da ta ganshi tun a gurin taron,kuma tana jin nauyin zuwa inda yake tunda ba kaita a kayi ba,don haka ta share duk da so da k'aunar da zuciyarta take taga a wani hali yake,don d'azun taga yadda idanuwansa gaba d'aya suka jirkice,Suna shiga da Aunty Maryam suka ci karo a babban tsakar gida,ta d'an fito shan iska,fad'a sukayi da Daddy akan zai k'ara aure inda tayi tsallan bad'ake ta nuna bai isa ba,shikwa yace tayi kad'an ta hanasa aure,shine tayi zuciya ta had'o kayanta ta taho ita da Hidaya,Hibba kwa tace babu inda za taje tana tare da Daddynta Abbas kwa dama yabi bayan Abdul channai,dama haushinta Daddy yake ji don tun barin Nusrat gidan har yau ba su dawo dai dai ba,kawai yana danne zuciyarsa ne,RJ yasha matuk'ar wuya kafin ya samu ya saba da rashin Nusrat,Hajiyan Rj d'in kuwa babu lallamin da ba tayiwa Daddy ba akan ya hak'ura ayi bikin Rj d'in da Hidaya amman sam ya k'i yace a barta ta d'an d'ana yadda ta sanya zuk'atansu suma,a can gurin aikinsu Zulaihat ta mak'ale masa,nacin yau da ban na gobe da ban,kuma ya riga ya fito fili ya gaya mata gaskiyar bai jin zuciyarsa za ta numfasawa wata mace bayan Nusrat,amman tak'i rabuwa da shi ta bi ta kafe shi take so take auna,da matsawar Hajiya tayi masa yawa akan aure kawai sai ya hak'ura ya sallamawa Zulaiha,amman da sharad'in duk ranar da Nusrat ta bayyana zai aureta domin itace Muradin ransa,tace taji ta yadda ta kuma aminta inda aka sha bikinsu,Hidaya ta kuma saddak'arwar ta rasa RJ har abada kamar yadda tayi sanadiyar rasa junansu da sukayi,sai dai tasan cewa da sonshi da k'aunarsa za ta mutu,tunda gashi ta kasa saurarar kowa,kuma an koreta daga makaranta sakamakon sharrin satar amsa da aka yi mata,anan nadama ta kuma shigarta sosai,yadda taji ciwon sharrin satar da aka yi mata ina ga Nusrat da suka yiwa sharrin zubar da ciki,ta tabbata alhakin tane yake yawo da rayuwarta,don gashi kamar k'ara mata son Rj ake ta kasa bawa kowa dama,har Daddy ya ibar mata kwanakin da in ba ta tsayar da miji ba zai bayar da ita sadaka,wannqn dalilin ne ma yasa da Mommy tace taxo su tafi zariya ta biyota,inda Daddy yayi hanza da su yaci gaba da shagalin auransa. Wata iriyar zabura Aunty Maryam tayi da taga Baba,juyin da za tayi ta arci na kare tayi tun tub'e ta kifa akan hannunta aikwa ta saki k'arar tsurewa da ta azaba,Baba ya nufi gurinta yana. "Subhanallah,Maryam yi a hankula,nine dai ba wani kike gani ba." Girgiza mishi kai take tana jaa da baya,ta kasa magana ta kuma kasa tashi,Hidaya da taji k'arar Momyn tasu ta fito daga gurin Iya itama tayi tozali da Baba don ko da su Nusrat ba ta lura bata juya da gudu tana. "Iya Baban su Yayarmu,Baban su Yayarmu ne a tsakar gida." "Ke ba na son rashin hankali,wanda ya mutu yana dawowa ne banda sokarci irin naki,sai dai in gizo yayi miki ko alj.." Maganar tata ka karewa tayi,yayin da tayi tozali da idon Baba ya shigo gurin da sallama, wani irin juyi tayi za ta koma d'aki sai ji kike k'umm ta k'ume da bango. "Yi a hankali Iya nine ba gamo kikayi ba." Cewar Baba yana nufar gurin da take ai sai ta k'ara gigicewa ta nufi d'aki,sai dai ina,ai Hidaya ta rufe ta saka sakata,girgiza k'ofar Iya ta shiga yi tana. "Dan Allah kuyu hak'uri,tsautsayi da k'addara ne yasa na kori Nusrat daga gidan nan,wallahi yanzu na canja halina,na daina kwad'ayi da son abin duniya." kafin ta fara karanto duk addu'ar da tazo bakinta,tana sakin fitsari da gudawa a lokaci d'aya,jin ihun Iya yasa Umma fitowa da sauri don ganin abinda yake faruwa garin sauri ba ta kula da b'awon ayabar da taci ta hullar ba ai kwa tayi sufa k'afarta ta tale sai ji kika b'as aikwa ta saki K'arar azaba. Aunty Maryam gocewar k'ashi tayi a hannunta,Umma kuwa karyewa tayi a cinyarta,Iya kuwa goshi yayi suntum abin tausai,har suma tayi kafin kuma su fahimci cewar Baban ne da gaske ba gamo sukayi ba,Yusra kuwa tasha dariya son ranta don babu wanda ya bata tausayi cikinsu,gaba d'ayansu babu wanda ya iya had'a ido da Baba,har Baffa Shamsu da ya shigo,matuk'ar kunya da nadamar da ba ta da amfani suke yi,kafin su shiga neman yafiya da duk abinda suka aikata,sun karb'i kuskuransu kuma suna fatan su gyara shi a nan gaba,ko bai gyaru gaba d'aya ba,yayin da Baba ya nuna musu babu komai,komai muk'addari ne daga Ubangiji,mutum bai isa ya sauya k'addarar da ke rubuce cikin littafin kowa ba face sai abin nan dai da alk'alami ya rubuta,suka nemi yafiyar Nusrat ma ta nuna babu wanda ta rik'e a ranta Hidaya kuwa kasa had'a ido tayi da Nusrat a hakan ta nemi yafiyarta,ta nuna mata babu komai ba ta rik'i kowa ba amman ba za ta manta da darasin da suka koya mata ba. Baba fad'a ya yiwa Aunty Maryam sosai da yaji dalilin zuwanta, inda yace a washe gari ta had'a kayanta ta bar gidan,to kuma sai ga Rj da Hibba sunzo washe garin, inda suka rankaya suka juya gaba d'aya,ta hak'ura ta saduda za taje ta rungumi k'addarar kishiyar da ta shigo rayuwarsu, Nusrat sun gaisa da Rj sun kuma tattauna bayan saduwa,kowa yaji abinda ya kasance da d'an uwansa bayan rabuwa,na jajantawa suka jajanta na murna suka taya juna murna,sai dai bai ji dad'in rasa Nusrat da yayi har abada ba,amman hakan bai hana yayi mata murnar auran da tayi ba,musamman da yasan wanda ta aura mutumin kirki ne na bugawa a jarida,ta riga kam ta gama dacewa,kamar yadda yake da yak'inin samun Nusrat d'in da Aashiq ya dace cikin masu dacewa. Hibba tayi murna sosai da ganin Nusrat da Yusra,don ta so ta zauna amman saboda makaranta babu yadda za tayi... [6/29, 7:42 PM] Rabi: 52 Kasancewar ba wani bincike za'ayi ba dukkan wasu shaidu da hujja suna hannu kuma dukkaninsu sun amsa laifinsu ba wata doguwar shari'a akayi ba aka yankewa kowa hukunci dai dai da abinda ya aikata,an kamo wa'yanda suka kashe Baffan Aashiq da wa'yanda suka kashe Falisha an yanke musu hukunci kisa ta hanyar rataya,Baffa da Baffa k'arami da Aasad d'aurin rai da rai,Mami ma kisa ta hanyar rataya,likita kuwa shekara goma gidan kaso,bayan an koreshi daga aiki,yadda ko nan gaba ba za'a kuma d'aukarsa a wani guri ba. Rayuka gaba d'aya babu dad'i,don kuka sosai sukeyi yayin da 'yan sanda suka kad'a kawunansu za'a fita da su,kuka sykeyi na tarin nadama,nadamar da ta riga tazo musu ak'urarran lokaci,musamman Mami ita da ratayeta za'ayi haka 'ya'yanta da 'yan uwanta suka rungumeta suna kuka itama tana yi tana kaico da zuciyar da ta bata shawarar da ta aikata hakan,tana jin inama baya za ta dawo ta samu damar gyara kuskuranta sai dai ba za ta tab'a dawowa ba idan ta wuce ta riga da ta wuce har abada,babu wanda ya isa ya juyo da ita. Aashiq bai so 'yan sanda suka shigo cikin lamarin ba,da yasan haka abin zai kwab'e tabbas da bai bari an kama Aasad ba,don silar kama shine hakan ta faru,ya riga ya yafe musu gaba d'aya babu wanda ya rik'e a ransa, da saka hannunsu ko babu idan Allah ya tsaro rayuwarsa haka za ta kasance bai isa ya sauya hakan ba, iya abinda yake rubuce cikin k'addarar rayuwarsa iya abinda zai samesa,masoyi ko mak'iyi babu wanda zai sauya masa komai sai abinda Allah ya zartar a kansa,dama can haka Allah ya tsaro rayuwarsa zata kasance tun fil azal,shiyasa yake ta tausar Asghar da yabi ya sanyawa ransa damuwa,shi da Hajja,ba zab'insu bane Baffan ya kasance haka ba,su godewa Ubangiji ma da suna da damar ziyartarsa a duk sanda suka so,ba kisan gilla za'a masa kamar Mami ba,kuma yana da damar da zai gyara tsakaninsa da Ubangijinsa,da kuma yafiyar wa'yanda duk ya b'atawa ma. Hajjaju ganin rayuka duk babu dad'i kowa yana jimamin abinda ya faru,kawai sai ta fasa shagalin bikin da tace daa za'ayi ta tura gidan su Nusrat,suyi walimarsu washe gari za'a zo d'aukar amarya,don taga alamun Aashiq d'in shi kansa yana buk'atar matarsa,duk da ba zuwa yayi ya gaya mata ba amman ta tabbata yana son kasancewar wani kusa da shi a halin da yake jin zuciyarsa kawai yana sharewa ne da mazewa,kamar yadda kwa tace d'in anyi walima a gidan su Nusrat,an d'an tara mutane ba laifi,don kowa ya san da auran nata,Hidaya da Hibba sunzo,har da matar RJ,Aunty Maryam babu dama ana can da hannu ya kuma suntumewa,gashi washe gari tarewar kishiyarta,walima ta k'ayatar,da daddare kuma aka zo d'aukar amarya,bayan tasha nasihu nasu ratsa jiki a a gurin Baba kana aka wuce da ita. Tun a ranar da suka wuce da Baba ya dinga kiran wayarta ba ta shiga sai a washe gari ya sameta,shine yace ta dawo haka domin yana buk'atarta kusa da shi ainun,ita kuma ta nuna masa baza ta iya tahowa ba tunda dama ba kaita akayi ba aure kawai aka d'aura,kuma Hajjaju tace sai komai ya nutsu za'a zo a d'auketa,yace tunda an riga an d'aura aure,kawai ta tawo shi yana buk'atarta ga Khalil nan zai zo ya d'auketa,ita kuma fafur da Khali in yazo tak'i binsa,shine yayi zuciya ya k'yaleta,duk da azabtuwar da rashin nata yake k'arawa zuciyarsa, bai san da labarin cewar yau d'in za'a kawo ta ba,tun safe da yaje ya dubo jikin Asghar ya dawo ya haye samansa bai k'ara sakkowa ba,sai da Hajjaju ta kirashi a waya da daddaren bayan 'yan rakiyarta sun tafi akan ya sakko tana son ganinsa,tunda ya fara sakkowa daga benan yaji zuciyarsa tana wani irin numfasawa jikinsa ya bashi Nusrat ce kafin idanuwansa su sauka a kanta tana zaune kusa da Hajjaju kanta lullub'e da mayafi,wata sanyayyar ajiyar zuciya ya saki kana ya zauna a saitin kujerar dake kallon wacce suke zaune,har lokacin idonsa yana kanta yana jin yadda zuciyarsa ke yamutsawa tana samun nutsuwa,tun da ya fara sakkowa zuciyarta ta fara dokawa kafin hancinta ya shak'o mata turaransa mai sanyata nutsuwa,wani irin dokawa zuciyarta take da k'arfi tana jin son ganin kyakkyawar fuskarsa da rayi missed kwana biyu.Nasiha Hajjaju tayi musu sosai kafin ta tashi tayi musu sai da safe tayi shigewarta d'aki,tana jin kewar Nusrat d'in,duk da a cikin gida d'aya suke,dad'inta d'aya ma tace a tawo da Yusra su dinga kwana tare don ba ta jin za ta iya kwana ita kad'ai yanzun,Yusra kuwa murna kamar me za ta zauna cikin gida d'aya da Yayarsu za kuma ta dinga shak'ar irin iskar da take shak'a. Cinyoyinta da jikinta ciwo suke mata sosai,kusan kwana hud'u suna abu d'aya,ita tsoro ya hanata sakar masa jikinta,shi kuma tausayi da raunin da zuciyarsa tayi a kanta ya hana ya mata ta k'arfi,da ya d'auki hanyar za ta fara kuka tana zafi,yana dannawa za ta kauce har cewa take ya bata maganin bacci tasha in yaso sai yayi a haka,yace ina kika tab'a jin inda akayi hakan?Sai a kwana na biyar Allah ya bashi sa'ar maidata cikakkiyar mace,kasancewar duk ta raba zafin,sai abin yazo mata da sauk'i. Wanka suka fito a tare zuciyar Aashiq fara k'al kamar takadda,yana jin yadda so da k'aunar Nusrat d'in ke k'ara samun guri a zuciyarsa yake zama,ita kwa Nusrat dad'inta d'aya ta wuce gurin,don tasha muguwar azaba,bacci kwa ishashshe ba ta samunta,wani zubin sai ya hak'ura ya k'yaleta tana tsaka da bacci za tajisa yana yayyamutsata,kan na shanunta kuwa da cinyoyinta wani irin azabar ciwo suke mata,tare suka shirya bayan ya busar mata da gashinta ya taje ya had'e mata shi guri d'aya,suka sauko k'asa don yin Break,sun san su Hajjaju sunyi nasu sun gama su kad'ai zasui budirinsu, Yusra ta d'ebo kayanta daga gidan Kawu Iliya,daga shi har Aunty Hafsa ba suji dad'in tafiyarta ba,sai dai ba suce da ita komai ba,tunda sun riga da sunsan shak'uwa da k'aunar dake tsakaninta da Yayarsu ko sun hanata tafiya ma baza ta sauraresu ba. Rayuwa suke mai dad'i da nutsuwa,a kullum jin son junansu suke yana k'ara k'arfi yana neman tik'ewa,ya fahimceta ta fahimcesa sai suke bin juna yadda suke suna kuma samun fahimtar juna,sun kuma sabawa da juna wanda rabuwa baza tazo musu da sauk'i ba,sun riga da sun zamo duniyar junansu. Duk wani abu da Aashiq yasan zai sanya Nusrat farin ciki shi yake,burinsa yaga dariyarta ko farin cikinta,shiyasa yake k'ara gudu cikin jininta wanda ba ta isa ta dakatar da hakan ba don ya zamo jini da jijiyarta,ya kuma yin babakere cikin zuciyarta ko guri d'aya bai bari wanda wani zai samu damar shiga ba,yabi ya cika ko ina amman a hakan kullum k'ok'arin yin abinda zai k'ara shiga zuciyarta yake,bayan bai bar wani fili ba,shiyasa wani zubin takanji kamar zuciyarta zata fashe saboda k'aunar Aashiq, gidansu gaba d'aya ya saka aka rushe aka d'ora sabon gini,phart d'in Baba da ban na Iya da ban,na Baffa Shamsu da ban,sai nasu da ban,ko da sun zo kwana gida, a phart d'in Baba Umma ke zaune ke jinyar k'afarta,da kullum take k'ara baya ba gababa,sai 'yar k'anwarta ce ke zaune ke jinyarta. Yusra kawai suke jira takaddunta su fito su tafi Lakshdweep,acan dukkaninsu zasu cigaba da karatu yadda zasu fi saurin gamawa suja ragamar company da hannunsu,don ayyukan sunwa Asghar yawa musamman yanzu da yake kamar wani mara lafiya don abinda Baffansa yayi ya tab'asa yadda bakwa zato,duk da Aashiq d'in yana tayasa da wasu abubuwan,damuwar Nusrat yanzu d'aya ce Shukhura,sai yaushe ne za ta waiwayesu?a kullum ne sai tayi kukan rashinta kusa da su,tana so ta dawo garesu ko zata samu damar cika alk'awarin da ta d'aukarwa Mama na kula da su,shiyasa a kullum take jin ciwon rashin sanin me yake faruwa cikin rayuwar Shulhuran,kulkum kukanta da adduarta Allah ya dawo da Shukhura cikin rayuwarsu,rashinta yana mugun tab'ata musamman a 'yan kwanakin nan da take yawan mafarkin Mamansu tana kuma jaddada mata alk'awarin da ta d'aukar mata. A matse Shukhura take ta kammala exxam d'in da ta rage musu ta taho zariya,burinta da nutsuwarta ta sanya Nusrat da Yusra cikin idanuwanta, don tun kwanaki Hidaya ta gaya mata cewar Nusrat d'in ta bar gidansu ta koma zariya,ta rasa me ya hau kanta ta manta da su,tayi watsi da rayuwarsu,ta manta su d'in jininta ne,Umma kawai take kalla kamar mahaifiyarta Nimha 'yar uwarta,a ranar da suka gama exxam d'in ta,matsawa Mustapha sai ta tafi zariya,babu yadda baiyi da ita ta bari ya kammala aikin da yake gabansa sai su tafi tare tak'i don kuka ta sakar masa bazai gane yadda take jin zuciyarta da ranta ba,hakan da ya gani ne yasa ya cewa Najib direbansa ya kaisu,don babu yadda zaiyi amman zaiyi kewarta ita da Amna,'yar da ta haifa kenan wacce taci sunan Mama,har ta yayeta k'aramin ciki ne yanzu a jikinta,yadda taga gidan nasu ya sauya sai ta shiga wasi wasin ko an siyar da shi ne,don ta kwana biyu rabonta da zariyan,fitowar Baba daga cikin gidan ne ya tsayar da tunaninta,binsa take da kallo kamar wata sokuwa,kafin tace. "Baba" tana fitowa daga motar d'auke da Amna a hannunta,kafin ta murza idonta da d'aya hannunta kar taje gizo yake mata. Waigowa yayi yana kallonta kafin shima yace. "Shukhura." Tayi murna da farin cikin ganin Babansu yana raye bai mutu ba,inda suka shiga labarin bayan rabuwa,anan take jin cewar Nusrat tayi aure,wasu hawaye ne masu zafi suka biyo kuncinta,tana jin zafi da rad'ad'in yadda ta rasa abubuwa masu muhimmanci cikin rayuwar 'yan uwanta,ko dawowar Baban nan yaci ace ta sani,yaci ace wani ya kirata ya sanar da ita,amman da yake burin Umma kawai tayi ta turo mata kud'i sai ta manta da ita,ko Nimha ma yaci ace ta kirawota ta gaya mata,anan ta bar Amna tana ta zubawa Baba surutu shi kuma ya biye mata,yana jin ina ma Maimuna na raye tazo taga jikarsu mai kama da ita sak,ba iya sunanta taci ba har kamannin nata ta d'ebo,duk da yaga jikoikinsa na gurin Nimha sai yake jin wannan d'in ta daban ko dan ita d'in jikarsa ce shi da Maimunansa? D'akin Umma ta shiga dake ta fama da k'afarta da kullum cikin d'orata ake tana gocewa gashi tayi wani irin kumburi na ban mamaki,tana shiga d'akin kawai ta rufe Umma da duka ko ta ina,ko lura da ciwon k'afarta ba tayi ba ta dinga tattake k'afar, don yadda take jin zuciyarta babu abinda baza ta iya aikatawa Umman ba, ta saka tayi asarar abubuwa da dama wanda ba ta isa ta mayar da su ba, zuwan Yusra kawai take tunawa sanda Mamansu na asibiti, ihunta da Babaya jiyo ne ya nufo d'akin da hanzari,don har Asma'u me jinyar Umman Shukhura ta had'a tana jibga,da k'yar Baba ya janyeta yana tambayarta abinda ya faru. "Gata nan Baba,ta gaya maka da bakinta abinda tamun ta raba ni da 'yan uwana." Kuka Umma take sosai na azaba,tana jin gara kawai ta gaya musu abinda tayi ko ta samu damar neman yafiyarsu ko ta samu sauk'in azabar ciwon da k'afarta take mata,tana jin kamar alhakinsu ne,tana kuka ta shiga gayawa Baba sihirin da tayiwa Mama yayi sanadiyar mutuwarta da farrak'un da tayi tsakanin Shukhura,don kawai ta mori dukiyar mijin Shukhuran,to ga dukiyar nan ta mora shin me ta tsinana mata?a yawon bin boka duka suka tafi gashinan tana karb'ar hukuncinta tun a duniya kafin taje can,a sanda take fad'ar Nimha ta shigo,kud'i ne ya narkewa Saminu a kaa,komai da ya mallaka an siyar hatta gidan da suke ciki amman bai kai kud'in da ake binsa ba shine jiya police suka zo suka tafi da shi,duk abinda mahaifiyarta ta fad'a a kunnanta suka sauka,ta fashe da wani irin kuka zuciyarta tayi nauyi da me zata ji ina kuma zata saka ranta,hannun Shukhura Baba yaja suka fita don bai san me zai cewa Umman ba, kawai dai yasan k'arshen zamansu ne yazo don ya gama auranta har abadan abadina.... [7/1, 7:37 PM] Rabi: 53 Suna kicin suna had'a dinner ita da Yusra,a gaggauce suke yin komai kasancewar yamma ta kawo kai,kuma tasan Aashiq yana hanya,tun safe suka fice da Asghar,kuma ba ta samu wayarsa ba har yanzun,tana aikin tana tunanin ko lafiya ta jishi shiru haka,wayarta ce tayi k'ara,agaggauce ta k'arasa gurin da wayar ke ajiye don duk a tunaninta Aashiq ne sai taga number in da ba ta sani ba,a sanyaye tayi peaking in wayar,ba zato ba tsammani taji muryar Shukhura tace."Yayarmu." "Shukhura"Nusrat ta fad'a cike da shakkun ko ba dai dai kunnuwanta suka jiyo mata ba. "Na'am Yayarmu ina bakin estate d'inku." Lumshe idanuwanta tayi ta bud'e tana furta Alhmdlillahi cikin zuciyarta,kafin tace. "Ki jira yanzu za'a zo a taho da ke." Tana kawowa nan ta kashe ta fara lalubar number Khalili da yake ba tare suka fita da Aashiq ba,yana d'aga wayar ta sanar mishi tana da bak'uwa a babban gate,Allah Allah take taga Shukhuran tazo kar taje kafin zuwan Khalil ta bar gurin,don gani take kamar ba gaske ba,wai Shukhuranta ce ta kirata a waya,ta kuma tako inda take.Ita kanta Shukhura a gaggauce take taga anzo tafiya da ita, babu yadda Baba baiyi akan ta bari da safe tazo don ganin magariba ta kawo kai,amman ba ta jin za ta samu nutsuwar zuciya idan ba ta saka Yayarsu da Yusra a idonta ba, ganin ta kafe kawai yasa ya rabu da ita,don bai manta kafiyar Shukhura ba,in tace sai tayin nan sai tayi,duk abinda zaa mata sai dai a mata,daga k'arshe ma fitowa tayi daga cikin motarta ta tsaya tana baza idanuwa,da yake Najib bar mata motar yayi yabi ta haya ya koma,babu inda ba ta zuwa da mota kawai dai Mustaphan ba ya so tayi dogon tuk'iy.Ganin itama a mota take sai Khalil d'in yayi gaba yace ta biyoshi a baya,cikin Yusra da Nusrat ban san wa yafi matsuwa yaga Shukhura ba,Hajjaju sai kallonsu take yadda duk suka je bakin k'ofa suka tsaya suna jiran a danna bell,dukkaninsu sun mata uzuri,sun san ba laifinta ba ne,a kullum zaman jiran dawowarta garesu suke,tunda kwa ta dawo ba za suyi sakaci ba,zasu karb'eta su manta da baya su fuskanci gaba,a kusan tare hannunsu ya sauka gurin bud'e k'ofar bayan da aka danna bell d'in,sai dai suna bud'ewa fuskar Aashiq ta bayyana da ta nuna gajiyar da yake tattare da ita,hannun Nusrat kawai ya kama ya jata zuwa matattakalar bene,sai dai suna tafiya tana waigowa tana kallon k'ofa,murmushi Hajjaju tayi kafin tace. "Turaki" Waigowa yayi don sam bai lura da Hajjajun ba tsabar gajiyar dake jikinsa,so kawai yake ya jishi cikin ruwan d'umi ko gajiyar za ta saki. "Jiran zuwan Shukhura take,kada ka b'ata mata wannan damar." Cewar Hajjaju tana kallonsa, gajiyayyun idanuwansa ya sauke akan Nusrat d'in kafin ya juya ya tafi ba tare da yace komai ba, yana buk'atarta kusa da shi sosai,amman bai jin zai b'ata mata wannan damar kamar yadda Hajjaju tace,banda a gajiye yake zai tsaya yaga farin cikinta,domin dariyar Nuss dariyarsa ce farin cikinta farin cikinsa haka ma kukanta kukansa ne,shiyasa kullum yake da burin ganin farin ciki ya wanzu cikin rayuwarta. Bakin k'ofar ta koma suka dasa sabon zaman jira,k'ofar ma a bud'e take bayan shigowar Aashiq Yusra ba ta rufe ba,da ita da Amnan gaba d'aya suka bi suka cukuikuye suna ihun murna,sun rasa ina zasu tsoma ransu don dad'i,kafin su dawo kan Amna wannan ta d'auka wannan ta ajiye suna jin wani iri sai yanzu ta sansu,kamata yayi tun zuwanta duniya ta dinga ganin gilmawarsu har ta fahimci su d'in iyayanta ne,amman haka Allah ya tsara ba su isa su kaucewa hakan ba,Kallonsu Hajjaju take cike da sha'awa,soyayyarsu da k'aunarsu ta burgeta ainun,wacce ta raba soyayya da shak'uwar nan ta d'au alhakinsu,alhaki kuwa ba kad'an ba,tana jin da ace Allah ya bata zuri'a da yawa tabbas da irin wannan KATANGAR za ta gina a tsakaninsu. Sai da suka gama murnar ganin juna suka nutsu,kafin Nusrat ta raka Shukhura d'aki,Yusra kuma ta tafi da Amna,bayan ta raka Shukhuran d'aki tace ta kimtsa kafin itama ta haye sama,sanda ta shiga d'akin sai a sannan ya fito daga wankan,ta baya ta rungumeshi,daga yadda yaji rungumar yasan yau Nunus d'insa farin ciki ya cika zuciyarta,zago da ita yayi gabansa yana ganin yadda murmushi ke kwance saman fuskarta,lumshe idanuwansa yayi yana kuma warasu akan fuskarta da tayi mishi kyau,har zuciyarsa ta fara wani irin yamutsawa,rungumeta yayi tsam yana shin shinar wuyanta,yadda take cikin farin ciki ya tabbata zai samu kanta fiye da yadda yake zato,yadda taji yana kuma matseta cikin jikinsa yana shin shinar wuyanta da k'irjinta yana wani lumshe ido tasan akwai bayani,sai ta fara d'an jan jikinta tana fad'in. "K'auri fa nake." Bakinsa kawai ya saka cikin nata ba tare da ya bata amsa ba,kafin ya d'auketa ya nufi gado da ita,d'an dukansa ta fara yi tana."Sallah fa za'a kira." Inaa ai sam ba ya sauraranta bare yasan me take fad'a. Sai da sukayi sallar isha'i kafin su had'u dukkaninsu akan dining,d'aukar Amna Aashiq yayi yana jin son ganin jininsa shima,aikwa ta shiga zaro masa zance,shi kuma yana biye mata,sun gaisa da Shukhura sosai a ranta tana yaba kyau da tsarin mijin Yayartasun don tayi kyahun dace kamar yadda shima ya dace,bayan gama cin abincin nasu kafin ya tashi Shukhura ta rok'eshi akan ya bata aron Yayarsu su kwana iya yau kawai,bazai iya hanata ba don ya tabbata itama Nusrat d'in za ta so hakan,amman ya tabbata zai mugun azabtuwa kafin gari ya waye,ya riga ya saba bacci a jikinta yana jinsa jikinta ba ya sanin sanda bacci yake saceshi,amman idan ba ta kusa da shi ba ya wani samun isasshen bacci,d'aga mata kai yayi kafin ya kalli gurin da Nusrat d'in ke zaune yayi mata kallon da ita kad'ai tasan ma'anarsa. Raba dare sukayi suna hira,kowa yaji abinda ya faru da d'an uwansa bayan rabuwa,akan filo d'aya suka kwanta duka su ukun,suka saka Nusrat a tsakiya kamar yadda suke a gida,suna jin inama baya ta dawo suga Mamansu tare da su. Takaddun Yura sun fito,suka fara shirye shiryen tafiya,sunje gogel sun musu sallama,su Baffa Ibrahim da kakannin Aashiq kamar su lashe Nusrat don so da k'auna,haka ma mahaifan Baffa k'arami,da har yau suke jin ciwon abinda d'ansu ya aikata,ranar da sukaje gidansu sallama take jin Umma na asibiti k'ashin k'afarta ya rub'e za'a yanke mata k'afar kuma babu kud'in yi mata aikin,da ta koma gida sai ta bud'e gurin da take ajiyar kud'in da Aashiq ke yawan bata,kuma ita ba taga amfanin da za tayi da su ba komai na more rayuwa akwai shi tattare da su babu abinda ta nema ta rasa,idan ta nema d'inma zai siya,tambayarta yayi abinda za tayi da kud'in shine take gaya masa,yace ta ajiye kud'inta,a ranar suka je asibitin ya biya kud'in,kuka Nimha ta dinga yi tana yi musu godiya,Shukhura da taji labari ta dinga yiwa Nusrat banbamin me yasa ta biya,ai da ta bari duka k'afofin sun rub'e sai aga k'afar zuwa gurin boka,Nusrat tace."Ai yanzun ma idan tana da hankali,ya kamata ta hankaltu,kuma ni don Nimha nayi,ko yaya ne mahaifiyarta ce,kuma tana son kayarta domin ba zab'inta bane mahaifiyarta ta kasance a haka,don da zab'inta ne na tabbata baza ta tab'a d'aukar Umma a matsayin mahaifiya ba,Shukhura kowa da zab'i ake bar masa bazai tab'a d'aukar bara gurbi cikin zuri'arsa ba." "Hakane Yayarmu,nima naso yi don Nimha,amman idan na tuna abinda ta mana sai naji na kasa,amman na gayawa Mustapha yace zai biyawa Saminu bashin a sakesa" Sai a lokacin Nusrat taji abinda ya faru da Saminun don daa ba ta sani ba,inda ta k'udirce a ranta bayan fitowarsa za tayiwa Asghar magana a bashi wani aikin a company,domin Nimha ba abin yarwa bace a gurinsu,'yar uwarsu ce jininsu ce basa bambamta ta,ko a daa ma mahaifiyarta ce ta janyo bam bamci da Nimha ta gane don kanta take neman kusanci da su. Ranar laraba jirginsu ya d'aga zuwa Lakshdweep,sati guda da zuwansu aka gama hada hadar komai abu na kud'i nan da nan suka soma karatunsu cikin kwanciyar hankali.... [7/1, 10:26 PM] Rabi: 54 Bayan shekaru biyar,sun kammala karatunsu cikin nasara,har lokacin haihuwa shiru babu labari,duk da so da k'aunar da suke na ganin jininsu basu sanyawa ransu damuwa ba,tunda duk sun tabbatar lafiyarsu k'alau,sun tabbata komai lokaci ne idan akwai a rubuce zasu haihu to zasu haihu d'in,idanma Allah bai basu ba zasu rungumi k'addara ba zasu butulce mishi ba,may be ba alkhairi ce garesu ba shiyasa bai basu ba,da Shukhura ta haifi cikin jikinta mace ta haifa me kama da Nusrat sak,wani ma zai iya rantsuwa Nusrat ce ta haifeta,kuma sai ta yiwa Nusrat d'in takwara,tana yin arbain suka taho lakshdweep ita da Mustapha suka kawo musu little Nusrat suka gani,da suka tashi tafiya anan suka baro musu Amna,sai ta k'ara raya musu gidan suka sanyata a makaranta,kafin su tashi dawowa taje primary 3 in yaso in suka dawo sai ta d'ora daga inda ta tsaya. Sai da suka jira suka harhad'a takaddunsu,kafin su wuce yawon k'asashe kana suka yada zango a saudiya don sauke farali,a can suka had'u da Baba da 'yar matarsa Aunty Shafa, bazawara ce ya samu yayi wuff da ita,gata da kirki sosai da son jama'a,duk shekara sai sunzo aikin Hajji wanda Aashiq ne ya d'auki nauyin hakan,Iya ma tazo shekaru hud'u da suka wuce,yanzun ma don k'arfinta ya jaa ne,inda Shukhura ta dinga yi mata tsiyar cewar,gashinan dai su da ta tsana ta tsani mahaifiyarsu gajiyarsu take ci,wacce ko mahaifiyarsu ba ta samu damar ci ba,Nusrat d'in da take cewa 'yar aljanu gashinan tana cin arzik'inta bayan duk cin kadjin da ta mata ashe a sanadinta za taje ta sauke farali, iya sai dai tayi shiru tana jin kunyar abinda ta aikatawa jikokin nata da kulluum cikin rok'ar yafiyarsu take kafin ta gangara,harma da 'ya'yan nata,tana k'ok'arin gino musu KATANGAR da ba ta ginota ba tun suna yara. Suna dawowa suka fara jan ragamar company d'in,nan da nan suka fara bunk'asa,rayuwa ta k'ara yi musu dad'i,ga Amna da ke hannunsu,da gaske dai Shukhura ta bar musu ita halak malak,inda suka sanyata taci gaba da zuwa makaranta anan,duk wani hutu da su Shukhura zasu samu gurin aiki,gidan Yayarsu take tarewa har Mustapha ya gaji yake biyota,da yake yana da hak'uri,kuma zuciyarsa ta riga ta raunata sosai duk wani abu da Shukhura take so shi yake so,ko baya so zai fara sonsa daga ranar da yasan tana so,muk'ullin kusa da nasu Aashiq ya basu suke sauka idan sun zo,da yake sun koma can kusa da gidan Asghar,dama gidan nasu a jere yake su uku,da nasa da na Asghar da Aasad,sai ya basu na Aasad d'in,da yake sun baro gidan Hajjaju,sai su Baba Azumi suka koma can,zaman Nusrat da ita,yasa ta jin baza ta iya zama ita kad'ai ba,Yusra a sha ruwan tsintsaye take mata,su Baba Azumi na dawowa ita da Baba Hadiza,ta sulale ta dawo gurin Yayarsu,da yake anyi bikin Faiza da Khalil shekaru biyu da suka huce, suma dai suna cikin estate d'in da zama. Shukhura ce ta matsawa Nusrat da cewar,tana yi mata alamu da masu ciki,anya kuwa ba ciki ne da ita ba?Nusrat tace ke ba likita ba bare nace kin gano kawai dai idonki ne ke nuna miki haka,Shukhura sam ba ta yadda ba sai da ta tilastata yin fitsari ta bata,ta siyo tsinke ta gwada,sai ga rad'a rad'an jan layi biyu,rawa sosai Shukhura ta hau tik'a,yayin da Nusrat sam tak'i yardar cewar ciki ne a jikinta,Aashiq Shukhura ta fara kira ta gayawa ma,da yake baya nan sunje Abuja shi da Asghar,suna shirin bud'e wani companys,d'inne,daga Aashiq sai ta kira Baba,sai Hajjaju na zaune,ba ta wani takwar kwashe ba har yanzu da d'an k'arfinta da yake an taso da farcen susa,su Baba Azumi kawai sai gani sukayi tana girgid'a kai suka tambayi ba'asi ta gaya musu,suma sai suka,hau murna da farin ciki,yayin da Hajjaju ta kira wayar Baffa Ibrahim ta gaya masa nan da nan suma suka hau murna suna masu mik'a godiyagurin Ubangiji da ya amsa musu addu'arsu, Aashiq kuwa yana gama waya da Shukhura ya kira Nusrat don yaji ta bakinsa don yasan halin Shukhura za ta iya d'ibarsa,duk rashin son maganarsa idan suka had'u da Shukhura sai ta sakashi,ga copynta nan kuma a gurinsu Amna,idan ya dawo bakinsa ba ya shiru har sai tayi bacci,ta sanar masa fitsarinta ta gwada ya nuna tana da cikin,amman ita ba ta wani yadda ba,yayin da Aashiq ya shiga nuna zallar farin cikinsa da kuma mik'a godiyarsa ga Ubangijinsa. Kamar jira ake asan da zaman cikin nata ta fara laulaye laulaye,inda sukaje adibiti gwajin farko ya nuna tana da ciki har ba tsawon wata uku,farin ciki gurin Aashiq kamar a sannan yasan da zaman cikin,a ko da yaushe idan suna tare hannunsa yana k'asan cikinta yana jin d'umin gudan jininsa,ashe shima zai haihu,ashe zai zamo uba,ashe zai ga gudan jininsa,ashe shima Allah zai bashi farin cikin da ko wani bawa ke sani yayin da ya azurtashi da samun d'a. Ni ban san wa yafi bawa Nusrat kulawa ba tun daga samun cikinta har ya tsufa,Aashiq dai yace kowa sai dai ya biyo bayansa,tunda cikinta ya tsufa Baba kullum sai yazo ya kawo mata rubutu da kansa ya zauna ta shanye sannan zai tafi. Kowa idan yaji cewar Nusrat ta haifi 'yan biyu sai yayi mamaki,saboda cikinta baiyi girman da zakayi tsammanin biyu ne a ciki ba,farin cikin da ke zuk'atan bayin Allah nan bazan iya rubuta muku shi,anyi hidimar suna,anyi shagali babu kama hannun yaro a sunan twince,musamman dama da ba wani shagli akayi ba a bikin nasu,Hidaya da Hibba sunzo,saura wata biyu bikinsu,tare za'a had'a,Daddy ya gaji da ajiyarta ya bawa abokinsa ita, Nimha ma tazo tun ana ya jibi suna da 'ya'yanta uku biyu maza mace d'aya,Amima ma tunda akayi haihuwar tazo,da yake mutuniyar Yusra ce,sai dai har yau Amiman babu wani k'wak'k'waran saurayi da ke zuwa gurinta. "Wai ke Yusra jik'aki zanyi ne na shanye,duk wanda yazo da sunan yana sonki sai kice,ba kya so?" Nusrat ce ta jefowa Yusra wannan tambayar,yayin da Yusran tace. "Ni da zaki jik'ani ki shanye d'inma da na huta kullum da tunanin yin nesa da ke." Takai k'arshen maganar tanawa Ashna da Ashfaq wasa da sukayi b'ul b'ul da su kamar ba 'yan wata hud'u ba,harara Nusrat ta zabga mata kafin tace. "To shikenan zan bawa Ya'u ke,kinga kin huta gani gaki" Direban Yusra ne Ya'un,yana mugun sonta,shiyasa basa shiri kullum cikin zaginsa take. "Ba sai an bawa Ya'u ba gani ina so,babu wani tunanin yin nesa da Yayarmu." Cewar Asghar yana shigowa ciki. "Hala da wasa kake don ba da ni za'ayi wannan d'anyan aikin ba,da wani idon kake son na dubi Ramla?" "Da idon da kike dubana kullum." Cewar Ramla itama tana shigowa ciki,ganin haka yasa Yusra ta d'auke Ashfaq da Ashna ta silale ta bar falon,da gaske Asghar yake yana son Yusra sai dai Nusrat,ta kafe ba za ta bashi ba,sai da Ramla ta sanya baki ta kuma gaya mata cewar tun haihuwar Safa da Marwa da tayi ta samu matsala a mahaifarta wanda da wuya ta k'ara d'aukar ciki,Asghar yana son Yusra ba ta isa ta hanashi sonta ba ko da ta hanashi auranta,kuma zai iya auro mata wacce ba ta sani ba ba ta san halayyarta ba gara Yusra ko ba komai k'anwarta ce,Nusrat ta nuna ba ta son su samu sab'ani ne don akan Yusra za ta iya sauka akan ko wani mataki, kar azo ana wallahi tallahi,sai da suka had'u su biyun suna bata baki,da k'yar tace za taji ta bakin Yusran idan tana sonshi za ta amince,idan ba ta sanshi baza ta masa dole ba,godiya suka yi mata don suna da yak'inin cewar Yusran baza tak'i ba, don yasan tunin dama ya dad'e da fara gina kansa gurin Yusran shiyasa tak'i saurarar kowa. Wanka suka fito manne da juna,yana mata rad'a a kunne,kafin yace."Ashe dai yarona ne ya k'ara miki dad'i,shiyasa a kwanakin nan nake jinki har k'wak'walwata." Kaucewa tayi tana masa hararar wasa kafin tace. "Ko da yaushe dama hakan nake,kai kanka ka sani." Bakinsa yakai kan idanuwan nata ya mata kiss kana yace. "Na sani,ke d'in ta dabance,kullum kamar k'ara miki zsk'i ake,kina kaini duniyar da nake jin tamkar mu dauwama ko da yaushe a cikinta." Kafin tace wani abu suka ji muryar Shukhura tana k'walla mata kira. "Yayarmu" Kamar zata fasa gidan. "Innalillahi,shi kenan zaki mini wuyar gani" Cewar Aashiq yana dak'una fuska,had'e da matseta cikin jikinsa kamar Shukhuran ya gani zata k'waceta,dariya Nusrat d'in tayi,yace. "Au dariya kike?Wallahi da gaske nake idan Shukhura na nan ganinki wahala yakemun,sai munzo kwanciya,sai kuma ki fara wash na gaji." Yakai k'arshen maganar yana kwatanta tadda take,dariya ta kuma yi, da k'yar dai ta samu ya saketa ta sako doguwar riga ta fito,har lokacin Shukhura ba ta hak'ura da kiran sunanta ba,transfer suka karb'o sun dawo zariya da aiki daga ita har Mustaphan,murna Nusrat ta shiga taya ta,don tasan saboda ita ne ta nace sai da suka komo zariyan,anan Shukhuran take gaya mata tana da ciki,kema Yayarmu naga kamar ciki ne da ke? Nusrat tace."Ke dai ban san ta ina kike hangar ina da ciki ba Shukhura?" "Jikina ne ya bani kinsan ni dake Yayarmu abu d'aya ne,Allah ne yayi baza mu zauna a mahaifa d'aya ba." "Nidai duk randa Aunty Shukhura tazo Yayarmu daina saurarata kike duk tabi ta k'wace min ke." Cewar Yusra,yayin da Shukhura tace."Kuma babu yadda za'ayi da ni ba,munma dawo zariya da zama,Yaa Aashiq ma nan ya ganni ya k'yakeleni." Dariya Nusrat ta saki tana jin so da k'aunar k'annanta na k'ara gudu cikin jini da jijiyarta,hira suka shiga yi duka su ukun,yawanci duk hirar Mama suke,suna yi suna hawaye,sun yanke zasu gina masallatai da makarantu,Allah yakai ladan kabarinta,yayi mata sakamako da gidan Aljanna sakamakon irin tarbiyar da ta basu wacce itace suke rik'e da ita har yanzu,kuma da ita zasui amfani akan 'ya'yansu suma su gina musu irin KATANGAR da ta gina a tsakaninsu. ALHAMDLILLAH Kuskuran dake ciki Allah ka yafe mana,ya kuma had'amu cikin ladan gaba d'aya. Irin wannan KATANGAR nake son ginawa zuri'ata idan Allah ya nufa zan haifa,domin irinta ce mahaifiyarmu ta gina tsakanina da 'yan uwana,Allah ya biyata da gidan aljanna. Bintu Abba ina matuk'ar godiya,domin ke d'in ta daban ce,kinmin halacci,nima zan miki halacci,daga KATANGA kin gama siyan littafina zaki dinga karantashi kyauta,kuma da kuka sanya kud'inku kuka bani lokacinku na gode. NAGARTA WRITERS ASOCIATION Baffa K'aramihttps://www.instagram.com/tv/CfLq0VxgK_u/?igshid=YmMyMTA2M2Y=