🍂JAURO🍂 (MAI ANGUWA) Story & Writing By JIDDARH UMAR 🌟🌙🌙🌙🌙🌙🌙🌟 *🌙✨MOONLIGHT WRITER'S ASSOCIATION🌙✨* https://m.facebook.com/Moonlight-writers-association-109698351308376/ *'''We are the moonlight writers we shine all over the world.''🌍'* ✍️✍️ بِسم الله الرحمن الرحيم ~~~~~~~💞💞~~~ *Ban yarda wani ko wata ya daura min littafi a shafin sa ko ya mai da min littafi Audio ba tare da izini na ba* 01 Shigowar ta dakin yayi dai-dai da ɗaga kwalbar da tayi tana ƙoƙarin kaiwa bakin ta, Cikin matsancin sauri da zafin nama ta fisge kwalbar tayi jifa dashi,wanda yana dakar bangon dakin ya tarwatse ya tafe, Kallon ta take cikin mamaki da matsanancin tsoro tace"me nake shirin gani haka SUMAYYA,ba dai kashe kanki kike kokarin yi ba? Fashewa da kuka tayi"me yakawo ki a dai-dai wannan lokacin,me kika zo yi Salma? "Ki bani amsar tambayar dana maki tukunna,me yasa zaki kashe kanki,Alhalin kin san hukuncin wanda ya aikata haka ko a wurin Allah" Cikin gunjin kuka tace"eh kin faɗi gaskiya kashe kai na zan yi,mutuwa zan yi,gara na mutu kowa ma ya huta,idan na mutu ai shine nan" Ganin yanda take kuka ne yasa ta rungume ta "ya isa haka,ba ki bukatar mutuwa,rayuwa ce ta kamace ki ba mutuwa ba, me yayi zafi haka" Jan majiya tayi suna zama kan gado, *Salma,da in aure shi Gara na mutu,gara ace na mutu,in yaso Baba in gawata zai sa akai gidan sa sai akai "ta faɗa tana share hawayen idon ta. Dafe goshi tayi" Ohh My God,pls SUMAYYA not again,ina ce mun riga mun gama maganar nan dake," "Bamu gama ba Salma,in dai a kan Jauro ne bazamu taba gamawa ba har sai ranar da aka fasa wannan auren," "Wai ɗan Allah me matsalarki da Jauro ne da baƙi kaunar sa har haka,ni banga aibin yaron ba" Wani dan iskar kallo ta jefeta dashi"wai shin kinsan waye Jauro,?kin taɓa ganin shi ne? "Eh ko ba shi bane wani dan dogo fari haka ya nada saje" Wani uban tsaki ta buga,"to Sulaiman ne kika gani ba Jauro ba,nasan cewa Sulaiman yana da ɗan kyau daidai gwargwado,kuma ba Class dina bane shi,domin koyarwa yake a makarantar Secondary,amma wlh Gara na aure shi akan na aure Jauro " "To yanzun fisabilillahi in banda abinki me aibun shi waccan din" Ajiyar zuciya ta sauke idanun ta na ƙara taruwa da hawaye,"Salma yanzu ki kalle ni,ga kyau Allah ya bani,har iya kyau,ina da kyaun jiki,na kammala makarantar College of Education,aiki kawai nake jira,ga ni da samari manyan masu kuɗi,masu motoci,ina da burin auren Namiji kyakkyawa sosai,har balle irin na Novel wanda zaki ji su da kwarjini da kyau ga kuɗi,su juya yanda suke so,"ajiyar zuciya ta Kuma saukewa"nasan Baba ba wani mai kuɗi bane,amma yana da rufin Asiri,tunda duk wani bukarmu yana biya mana,amma shine wai ya rasa mijin da zai haɗa ni aure dashi sai wani bakin Fulani"nan take hawaye ya ɓalle mata. "Ban gane bakin Fulani ba" "Wallahi Jauro ko a cikin Fulani sai an bincika kafin a samu mai munin sa,baƙi ne shi sosai,gashi ba shida tsaye sosai,kullum cikin kaya daya yake,wata shegiyar bulun riga,wacce haɗuwa ta huɗu dashi amma da ita nake ganin shi," "To ai muni ba wani abu bane" Hararanta tayi"kawai sai na nuna ma ƙawaye na shi nace ga mijina,waiyo Allah,ke kinma San Bala'in Family su Jauro kuwa Salma,wallahi tunda nake ban taba jin fitina da tashin hankali ba irin na Ahalin su,ke ko a littafin Hausa,a haka zan yi fata kutsa kai na, Ni wallahi bana son shi,gashi ɗan ƙauye sai bakin iskanci ya tara" "To wai a ina shi Baba ya sanshi,nasan dai ba ɗan uwanku ba ne" "Haka ne Salma,amma duk yanda za'ayi ba zan taɓa yarda ayi wannan auren ba" "To ko zaki bani labarin shi,dan wallahi har na matsu naga wannan Jauro" Tsaki taja"ai kuwa da kin yi dana sanin ganin sa,kuma ni gaskiya ba ni da wani cikakken labarin sa" Bata fuska tayi "pls mana Sumayya ɗan Allah ki faɗa min" "Wallahi ban sani ba,sai dai in zaki ni ma da kanki,abu ɗaya kawai na sani a kanshi,shine shi ɗin mugu mugun Ɗan iska ne" Mikewa tsaye tayi"koma dai menene zan nimo Asalin labarin" "Da labarin sa da zaki nimo ai gara ki taimaka ki nimo min hanyar da zanbi a fasa wannan auren" Komawa tayi ta zauna tana kallon kawar nata"Sumayya"ta kira sunan ta, "Umm" Ta fada tana kallon ta. "In baki shawara zaki bi? " Me zai hana in na ƙwarai ne" "Me zai hana kibi maganar mahaifinki,ƙila wannan auren naki akwai abinda ya hango maki wanda ke baki hango ba,kuma kun san iyayenmu suna matukar sonmu ba zasu taba yi mana abinda zai cutar damu ba,please ki bi shawarata ƙawata" Sai da ta bari ta kammala tsaf,sannan ta zame hannun ta dake cikin na Salma, "Ke ƙawata ce wacce muka tashi tare tun muna ƙanana har muka girma,kusan ko wani lokaci muna tare," Lumshe ido tayi ta buɗe "Alhamdulillah,na godewa Allah daya nuna min Asalin wace ke,ashe Salma ba zama amana muke ba,Ashe baki ƙaunata, kina farin ciki da ci baya na,har kike ban shawaran auren Bafullatanin Ƙauye,in Allah ya yarda kamar yanda kike min fatan Auren Jauro sai Baban ki ya aura maki mutumin da ki kafi tsana a duniya,ki ji in da daɗi," Kallon mamaki take mata yanzun daga kyara kayanka sai za zamo sauke mu raba,ita da shawara ta bayar ba da wata manufa ba,riko hannun ta take ƙoƙarin yi,da sauri taga ta matsar da hannun ta, "Haba mana Sumaiya,yanzun kin min adalci kenan da irin wannan fahimtar da ki kai min," "Ni ma kin kyauta min kenan,kin ga ni bana son ma wata magana Salma tashi kawai ki tafi" "Yanzun korata kike Sumayya" Kauda kai tayi "kamawa yake yi" Ajiyar zuciya ta sauke, tana mikewa"to zan wuce kamar yanda kike buƙata," "Allah ya raka taki gona" Girgiza kai kawai tayi,ba damuwa,in dai halin Sumayya ce ai sai dai taba wani labari,ta san yanzun bata cikin daɗin zai,amma ta tabbatar da zuwa anjima da kanta zata zo gidansu bata haƙuri,ko kuma ta kirata a waya,shi yasa gara ta barta ta dawo haiyacin ta, Tana fitowa daga ɗakin Sumayya dakin Mama ta shiga,gaisawa suka yi, "Ya iyayen naki" "Suna lafiya Mama" "Kin ko ga kawar taki" "Eh Mama,dama kuma ina son in maka magana a kanta" Zama tayi bakin gado"zauna ina jinki" Zama tayi a kasa"Mama ɗan Allah kisa Baba ya fasa aurawa Sumayya wannan mutumin tunda bata son shi,Mama kinga kuwa yanda Sumayya ta rame,gabaɗaya ta fita hayyacinta " Dukar da kai tayi sai kuma ta kalle ta "ni kaina abun na damuna Salma,sai dai na rasa yanda zanyi,daga Sumayya har Mahaifinta taurin kai ne dasu,idan suka kafe akan abu sun kafe kenan,ita tace bata so,shi kuma ya rantse sai anyi,gabaɗaya na rasa yanda zan shawo kansu,ko abincin kirki Sumayya bata ci sai nayi da gaske,bansan ya suke so nayi da rayuwa ta ba" "Sai dai mu taya ta da addu'a,sannan dazu dana shiga kokarin shan guba take,dan Allah Mama a ƙara saka ido a kanta" Cikin tsoro ta dafe kirji "guba" Da sauri ta mike ta nufe dakin Sumayya,a zuciyar ta tana rayawa akan lallai duk yanda zata yi dole tayi domin a fasa wannan auren,tana ji tana gani ba zata yarda ta rasa yarta ba,koda kuwa sunan Baban su zata kai wurin Malami. *🍂JAURO🍂* (MAI ANGUWA) Story & Writing By JIDDARH UMAR 🌟🌙🌙🌙🌙🌙🌙🌟 *🌙✨MOONLIGHT WRITER'S ASSOCIATION🌙✨* https://m.facebook.com/Moonlight-writers-association-109698351308376/ *'''We are the moonlight writers we shine all over the world.''🌍'* ✍️✍️ بِسم الله الرحمن الرحيم ~~~~~~~💞💞~~~~~~~ *2* Salma bata jima da fita ba sai ga Mama ta shigo ɗakin da sauri tana ƙiran Sunan ta, Zabura tayi daga kwancen da take tana durowa daga saman gado "Na'am Mama" Tsayawa tayi a gabanta tana ƙare mata kallo,"in jin dai baki sha gubar ba" "Turo baki tayi ta koma ta zauna" Mama shine zaki ban tsoro da wannan kiran naki" "Kaniyarki,ina tambayarki kin tsaya min shirme,Ashe Sumaiya bakida hankali,yanzun saboda wani ɗa namiji tsinanne sai ki kashe kanki,yanzun kin min adalci kenan" Sai kuma ta saka kuka, Ganin mahaifiyar nata na kuka ne yasa da sauri ta taso ta rungume ta "ɗan Allah Mama kiyi haƙuri,ba zan ƙaraba,na ɗauka baki fahince halin da nake ciki bane ke da Baba shi yasa,ni kuma na rasa mafita,zuciyata zafi take min shiyasa na zaɓa wannan hanyar" "Waya faɗa maki ban fahince ki ba,a duniya a kwai wacce tafi cencenta ta fahimci ɗa sama da uwa,babu,na san komai na kuma san tunanin ki,dan haka kar ki kara yin irin wannan tunanin,dan in dai Jauro ne wannan auren kamar anyi an fasa" Kallon Mamaki take wa mahaifiyar nata"Mama taya hakan zai faru,bayan Baba yace mutuwa ce kawai zata iya dakatar da wannan auren,kuma naga kema da ki kai mai magana kin yarda yayi" "Ba ni nace ki kwantar da hankalin ki ba,ai in takamar shi taurin kai,bai fi karfin Malamai ba,mun riga munyi magana Hajiya Rahama,matar kansila na kasan layin nan,akwai in da zata kai ni,sha yanzun magani yanzun" Ɓata fuska tayi tana kallon mahaifiyar nata"Mama nifa tsoron zuwa irin wannan wurin nake,gaskiya karki je" Cikin masifa ta hayayyako mata"to shikenan na fasa zuwa,tunda dama ashe son shi kike ai dole ki ce haka,ke kika sani sai ki karata a can,ana mikin gudun wahala kina fadin tsoro kike ji,yanzun ke ko gidan Boka aka ce kije baki zuwa saboda wannan,sam ko tsari ba ku yiba,mutum tamkar wani Almajirin Ƙauye,ke kika sani"ta faɗa tana kokarin juyawa zata bar ɗakin. Cikin sauri ta riƙo ta"na yarda,in dai har za'a fasa wannan auren na yarda Mama kije,ɗan Allah ki taimaka min"ta faɗa tana zubar da ruwan hawaye daya cika mata ido Tsaki tayi"ni daɗi na dake saurin kuka,to ya isa,zuwa gobe da yamma zamu je" Gyaɗa kai tayi tana kara lafewa a jikin Mama. Ture ta tayi ta mike tsaye"ni ɗaga ni da wannan son jikin naki" "Mama ɗan Allah mana" "Ohh lallai yarinyar nan,kinga ni ina da aikin yi bari ma ki gani" Nan tayi waje abinta. Ajiyar zuciya ta sauke,yayin data koma jikin gado ta jingina bayanta ta lumshe ido, A baiyane tace "ya Allah ka raba ni da auren wannan bawan naka" Kara gyara zama tayi yayin da zuciyarta ya tafi tunanin farkon haɗuwar ta dashi,wanda ita tun a ganin farko wanda bata sanshi ba bai san ta ba,taji haka kurin mutumin bai mata ba,karamin tsaki taja,"kai Yawo ma dai bai yi ba a rayuwa,da ace ranar batayi Baba karyar zata taya Aunty Amina gyaran daki ba da haka bai faru da ita ba,da basu haɗu da juna ba,"a wannan ranar kuwa tana kwance ne a gida tana barcin asara,in ji ta,bata da in da zata yi,kawai sai ga kiran Rahina,cikin yana yi na mai barci ta ɗauka,wanda daga ɗayan bangaren tace"Sumayya kina ina ne? "Gida mana" "A'a baki samu zuwa bikin Rose bane,gashi har za'a tafi park " Zabura tayi ta duro daga kan gado,tana missike ido"ke wallahi na manta yau ne,gani zaune a gida dama babu wurin zuwa" "To ki dai yi sauri kam,dan ƴan makarantar mu ma duk gasu nan sun iso" Ihu tayi"ke ki ce yau da ansha dani,bikin Rose tamu gaba ɗaya ai ganinan zuwa"da sauri ta ajiye wayar, Fitowa tayi tsakar gida,tana niman ruwan wanka,sai dai duk durom din da suke ajiye ruwa ba komai a ciki, Tsaki taja"wai yo Allah na,to yanzun ina zan samu ruwan wanka " Ƙanwarta ƙarama ce ta shigo gidan da leda a hannun wanda daga dukkan alamu aikanta aka yi, "Yauwa ke Aisha zo nan" Zuwa yarinyar tayi ta tsaya "gani Sumayya" Harara ta dalla mata"wai me yasa yaran nan bakuda kunya ne,ke nafa na baki aƙalla shekara goma sha uku,amma shine ba ki iya ce min Aunty,sai Sumayya gatsau,in da yaran masu kuɗi suka fiku kenan,sai da kaji ance Aunty Baby,ko Aunty wacce,amma ku ya'yan talaka sai rashin kunya tsiya " Daga bayanta taji muryar Mama na faɗin "daɗin abin dai ubanki talaka ne,kin ga a rashin tarbiyar harda ke" Juyawa tayi ta kalle Mama tana turo baki"ni fa Mama da Aisha nake magana,ba ki ji wai Sumayya take kira na bancin na girmeta " "To sannan Uwar ta,ke zo nan oh,kyale ta" Da gudu kuwa yarinyar ta wuce tana mata gwallo. Nuna kanta tayi"ni ko,ni kike wa gwallo ko,dan kin ga Mama na ɗaure maki,zamu haɗu,ai zan kami ki " "In kin gama faɗa sai ki zo ki dibo mana ruwa a gidan Malam Sa'adu,tunda kin ga ko tarfe ba mu da shi a gidan" Zaro ido tayi tana kallon Mama kamar taga abin tsoro,domin a duniyar Allah idan akwai abinda ta tsana shine ace taje dibo ruwa,haba,haba,ai wannan ba ƙaramin zubar da Class bane,kamarta,yanzun ace kamar ta ce zata dibo ruwa kuma tun daga nan har bakin layin su gidan Malam Sa'adu,kawai sai a ganta da baho akai wai tana dibar ruwa,ai wallahi samarinta ma dariya zasu mata, "Mama dibar ruwa kuma,ɗan Allah ki saka su Abdullahi mana kin ga ni yanzun ma fita zan yi," "Wasu Abdullahi,yaran da basu nan,duk basu dawo makaranta ba,dan haka wa kike son in aika,gashi lokacin daura girki yayi,ai kema dai kin gani ba nida ruwa, mdan haka bana son wata doguwar magana,ina jiran ki" ta faɗa tana jan hannun Aisha zasu shiga daki,juyowa tayi"kar in ji kin bar gidan nan da sunan zuwa unguwa,kin dai san halin Baban ku in ba so kike ki saka ni cikin matsala ba" Hawaye ta fara,oh Allah me yasa ka yini a gidan iyaye talakawa,da yanzun ina Dubai ko London ina hutawa ta,ko kuma ina kan gado yana juyawa dani,sai kuma da sauri tace Astagafurullah, Daki ta goma ta ɗaki jakkanta wanda kayan kwalliyarta ke ciki,madubi ta dauka ta dauki man baki ta shafa,ta dauki ɗankwalin ta dake gefe ta goge fuskarta dashi tas, Jakkan kayanta ta buɗe ta dauki wani Les da Aunty Amina ta bata,ta saka ta yafa gyale, Ta windon dakinta ta lelleka tsakar gida,sai da ta tabbatar ba kowa sannan ta fito da sauri_sauri ta nufe kofar gida tana fita da sauri ta shige gidan makotarsu,har tana ba matar dake tsakar gida tana shara tsoro,waigen bayanta take"Sumayya lafiya,waya biyo ki " Itama juyawa tayi ta kalle bayan nata,"babu kowa," Dafe kirji tayi"wai har kin ban tsoro" Bata ce mata mo kai ba,sai butar data gani a tsakar gidan ta ɗauka,wanke kafarta tayi dashi,sannan ta koma saman dakalin kicin ta zauna,jakkan hannunta ta buɗe ta ɗauko wani karamin robar mai ta shiga mutsukawa a kafa da hunnu, Kallon ta matar tayi rike da baƙi "naga ta kaina,ƴan matan zamani sai da daka tsami,babu wanka" Kallon ta tayi"ba zaki gane ba maman Aminu,wallahi ba muda ruwa ko dis,yauwa Mama tace wai ɗan Allah ki ranta mata roban fenti guda ta fara aiki dashi,idan su Abdullahi suka dawo makaranta zasu dibo maki " "To ba damuwa gayacan ki ɗauka ki kai mata" "A'a idan dai kin samu yaro ki daura masa ya kai mata dan ni dai sauri nake yi" Kallon ta take"naga dai ta ƙofar gidan zaki bi ki fita ba sai ki mika mata ba" "A'a ta bayan gidan nan zanbi dan bana son saka ido irin na mutanen unguwar nan" Girgiza kai kawai tayi taci gaba da aikinta,dan in dai halin Sumayya ce sai dai taba wani labari, Tana gamawa ta tashi ta saɓa jakkanta,a yanda ta fito wata shar da ita ka ɗauka yar gidan wasu masu kuɗi ne,gashi dai ko kwalli bata shafaba,man baki ne kawai sai kamshin da take yi,yanda kasan wacce tayi wanka,"Maman Aminu na wuce" "Allah ya tsare" Tace tana mata fatan shiriya a zuciyar ta,mutane da dama suna mata kallon yar iska ce,saboda yawo da Shige shige irin nata,sai dai ba haka take ba,ita ta san halin yarinyar,sai dai rashin ji da taurin kai irin na ta,uwa uba rashin kunya,. *🍂JAURO🍂* (MAI ANGUWA) Story & Writing By JIDDARH UMAR 🌟🌙🌙🌙🌙🌙🌙🌟 *🌙✨MOONLIGHT WRITER'S ASSOCIATION🌙✨* https://m.facebook.com/Moonlight-writers-association-109698351308376/ *'''We are the moonlight writers we shine all over the world.''🌍'* ✍️✍️ بِسم الله الرحمن الرحيم ~~~~~~~💞💞~~~~~~~ *Ban yarda wani ko wata su ɗaura min littafi a shafinsu ko a mai da min littafi Audio ba tare da izina ba* *3* Kamar yanda ta faɗa haka kuwa akayi,ɗan ta bayan gida tabi,bata yarda ta biyo ta cikin unguwar su ba,sai bayan gidajen mutane data tabi,tana kwana,da haka har ta fito bakin titi, Bata wani jimaba a bakin titi ta samu abin hawa,"Malam Tunga zaka kaini,nawa" "Dari biyu" Waro ido tayi"dari biyu fa,sai ka ce zanbar gari,kaga ajiye ni a Mobile,tunda Saba'in ne" Kallon ta yayi daga sama har kasa"haba Hajiya,ai ba girmanki bane,kawai ke da zaki ce muje kawai," Hararanshi tayi"kaga in bazaka Tunga a dari da ishirin ba,ka sauke ni Mobile,shima in ba zaka ba,ka ƙara gaba" Girgiza kai yayi"shigo muje,amma dai dari da hamsin zaki bada " "Kai dai ka sani" ta faɗa tana shiga, Ita sai lokacin ma ta lura da ashe akwai mutum zaune a ciki,kallon shi tayi,wata kodaddiyar bulun riga ce a jikin shi mai dogon hannu,irin wanda yake da botiri a ƙarshen hannu, da wata baƙar wando irin wanda yawanci a gwanjo ake samun irin su,itama ta fara canja kala,sai talalmi cover shoe,wanda fatar takalmin ma ya fara tashi, Bayan ta gama kare ma kayanshi kallon ne ta maida idanun ta kan fuskarshi, Baƙi ne sosai,sai dai ba irin wuluk ɗin nan ba,gashin kanshi a cike yake mai laushi irin ma fulani,wanda shi kawai zai nuna maka cewa shi Fulani ne,ba shida wani dogon hanci,haka kuma bakin shi madaidaici ne,ba zaka kira shi ƙarami ba tunda yanada dan girma,kamar yanda idanun shi basuda wasu girma,kai a takaice dai yana cikin gerin mutanen da za'a saka cikin Babu Yabo Babu Fallasa,haka kuma ta bangare guda duk da a zaune yake ta tabbatar da baida tsawo, Yana juyowa kuwa suka haɗa ido da ita,ai kuwa harara ta zuba mashi tana matsawa gefe,dan ita kama yake mata ma yan kidnapping, Waya ce ta shiga kara babu kakkautawa,da sauri ya ciro wayar daga Aljihun shi,wanda ganin kalar wayar dake hannun shi ne yasa zarginta ya ƙara girma a zuciyarta wato ɗan Kidnapping ne,in ba haka ba ta ina kamar wannan bagidajen,ba ƙauyen za'a ganshi riƙe da waya IPhone kuma ba ƙarama ba,a ƙalla daga gani zatayi dubu dari biyu da wani abu, Receiving call ɗin yayi,ya saka wayar a kunne,sai dai cikin rashin sani hannun shi ya danna amsa kuwa, Kawai sai ji tayi daga ɗayan ɓangaren ance "Kai JAURO amma ka cika ɗan iska,shine zaka bani Condom marasa kyau" "Kamarya marasa kyau? " Eh mana ina sakawa ko gamawa banyi ba sai gashi abu ya yage,Allah saura kaɗan nayi ma Madam bari" "To killa dai baka saka da kyau bane Malam" "Wallahi sau uku kenan yana min haka,dan haka zan kawo maka sauran kwalen a canja min wasu,dama kwalli goma ne,to gashi ko daya bai kare ba" "To ba damu ka kawo min gida zuwa anjima, sai na canja maka da wani" "Yauwa na gode aboki na" Tsaki yaja yana kashe wayar. Ji yayi mai keken yace"Malam Condom kake sayarwa ne" "Eh ko zaka siya ne" Dariya mutumin yayi"ikon Allah,kowa da kalar tashi sana'ar,yanzun nawa kake samu riba a kwali daya" "Dari da hamsin mana," "AH lallai ba laifi,to yanzun ina son kwali biyu zan samu" "Me zai hana abu na kuɗi" Dariya suka saka a tare, Jin anja tsaki daga gefen shi ne yasa ya juya ya kalle ta,wannan karon ma hararan shi ta kuma yi, "Malama kwali nawa kike so? Ya tambaya babu alamu wani Dar a tare dashi, Zaro ido tayi har tana dafe kirji," Me kenan ? "Condom mana,kinsan yana da kyau ƴan mata su dinga amfani dashi saboda tsaro" Tunda take a rayuwarta ba'a taɓa faɗa mata magana mafi muni ba irin wannan,wani irin bacin rai ne ya sauko mata,wanda har sai da ta kasa magana, Kallon me Adaidaitan tayi cikin bacin rai"Malam sauke ni anan" Juyowa yayi "Amma kince Tunga zaki sauka ai,kuma gashi ko Mobile bamu kai ba" Cikin masifa tace"nace ka sauke ni,na fasa zuwa,ka sauke ni" Tsayar da Adaidaitan mutumin yayi, Cikin fishi ta fito"wato fatan iskanci kuke min ko,kai kuma harda cewa in siya Condom,to ta Allah ba taka ba,har in yi aure bazan taba yawon karuwanci ba sai dai kanwarka tayi" Gira daya ya daga"laifi ne ɗan na maki tayin abin arziƙi,waya faɗa maki yanzun akwai budurwa Virgin,duk yawancin ku ba in da baku leka ba,ni shawara na baƙi ko kwali nawa kike so zan saida maki,kuma zan maki ragi sosai " Tsabar baƙin ciki bata masan sanda tace"na leka harda dakin ubanka"ta faɗa tare da rarumo wani katon dutse dake gaban zata buga masu, Ai da mugun gudu mai Adaidaitan yaja Keken shi ya bar wurin,yayin da daga shi har me Keken suke kwasar dariya, Bakin cikin wannan abinda sukai mata ne yasa taji gabaɗaya ta tsani fitar da tayi,dan haka tare wani keken tayi wanda zai dawo da ita gida,in da anan ta zo ta tarad da Mama da Baba suna jiranta da wata masifar. Tana shigowa gida a tsakar gida ta iske su zaune har da Kannanta yayin da kwanukan abinci daga gefe alamun yanzun Baba ya gama cin abinci, Dukawa tayi ta na gaishe shi,tunda tasan irin wannan ranar baya jimawa yake dawowa "barka da dawowa" "Daga ina kika fito" "Baba naje gidan Anty Amina ne taya ta gyaran daki" "Da izinin wa" Kallon inda Mama ke zaune tayi,suna haɗa ido ta kauda kai, "Na faɗa ma Mama" Kallon Maman yayi"kika ce bata faɗa maki ba" Kallon Sumayya tayi,ita ma suna haɗa ido ta dukar da kai. "Oh ta fada min amma na manta ne" Hararan Sumayya yayi"tashi kiban wuri,ai na kusa maganin wannan yawon naki" Turo baki tayi tana tashi ta shige daki,tsabar bakin rai a ranar kashe wayar ta tayi, Sai kuma haɗuwar su ta biyu,wanda shima ba zata manta ba. Jin kiran da Aisha ke mata ne yasa da sauri ta dawo cikin haiyacinta tana kallon ta, "Wai Mama ki fito kiyi Sallah lokacin Magariba yayi" "To " Kawai tace tana mikewa. *🍂JAURO🍂* (MAI ANGUWA) Story & Writing By JIDDARH UMAR 🌟🌙🌙🌙🌙🌙🌙🌟 *🌙✨MOONLIGHT WRITER'S ASSOCIATION🌙✨* https://m.facebook.com/Moonlight-writers-association-109698351308376/ *'''We are the moonlight writers we shine all over the world.''🌍'* ✍️✍️ بِسم الله الرحمن الرحيم ~~~~~~~💞💞~~~~~~~ *Ban yarda wani ko wata su saka min littafi a shafin su ko a mai damin littafi Audio ba tare da izini na ba* *4* Washegari da safe misalin ƙarfe takwas na safe,a lokacin ta kammala haɗa masu abin ƙarin safe,tana sharan tsakar gida,sai ga yaro ya shigo da sallamah,amsawa tayi dan lokacin ita kadai ce a tsakar gida sai Aisha dake wanke-wanke,kasancewar ranar sati ce, "Wai ana sallamah da Sumayya" "In ji ubanwa da sassafen nan" "Yace ace Jauro" "Je kace tace ba zata zo ba,idan kuma ya isa sai yazo ya jani" Daga bakin kofar Baba taji ance"idan baki fita ba ni kuma a yau zan sa a ɗaura auren in yaso sai yaji daɗin cika umurnin ki,dan ba wanda ya isa ya dakatar dashi idan ya shigo daukar naki,koni nan ubanki ban isa in dakatar dashi ba,wanne kika zaɓa "Baba ya faɗa daga inda yake tsaye a bakin kofar dakin shi. Ba tare data ce komai ba,ta jawo wani hijabin Mama dake saman igiya, wuya ma ya mata yawa,har ana iya ganin suman kanta,da yake hijabin roba ne,ƙafarta silifas ne,kamar yanda take daure da zani iya kirji sai riga a sama,dan haka zanin bai gama sauka kasa ba,fuskarta kuwa yanda kasan anyi gobara haka yake, Kai tsaye kofar gida ta nufa, Yana tsaye a kofar gidan,sai dai wannan karon riga ce fara a jikin shi,amma daga gani ta gwanjo ce,dan har wani kaba kaba take yi,sai takalmi dai na rannan ne,wando ma dai ya canja,sai wata baƙar leda dake hannun shi, Cikin bacin rai ta tsaya a gabanci babu sallamar,har wani huci take,gashi har girgiza take, Kallon ta yake tun daga sama har kasa,yayin daya tsayar da idon shi a kanta,na wani lokaci,sai kuma ya dawo da kallon shi kirjinta,nan ma na wasu yan daƙiƙai,tabe baki yayi "Assalamu'alaikum" Ya mata sallamah. Abu ɗaya ne yasa kawai ta amsa mai sallamah shine sanin muhimmancin ta,shima a ciki_ciki ta amsa, "Me ya kawoka gidan mu da safe" "Nazo taɗi ne mana" Wani banzan harara ta zuba mai"a garinku hala da safe ake zuwa taɗi? Dariya yayi kaɗan "kusan haka,kinsan me? Hararan shi tayi tana jan tsaki, " Nifa gaskiya zan faɗa maki,dama kallon ɗan iska kike min,amma maganar gaskiya bai dace kina ɗaurin kirji ba,saboda hakan na zubar da nonon mace,kuma kin ga ni ba zan so haka ta faru dake ba" Kallon kirjinta tayi ta kalle shi,da sauri ta maida hannun ta cikin hijabi tana karewa"ai ba kallon da nake maka kenan ba,haka din yake kai cikakken ɗan iskan ne,in ba haka ba me yakai idanun ka wurin" Ɗan shafa kanshi yayi"nifa ba ɗan iska bane,tunda ban taɓa iskanci ba,sai dai lokacin da naje England ne ƴan matan garin suka so lalatani,da kyar dai Allah ya kwace ni kuma.... "Kai dai ɗan iskan ne,a ina ka taɓa zuwa England,kuma ka rantse da Allah baka taɓa iskanci ba,tsakaninka da Allah"ta faɗa tana kafe shi da ido. " Eh to ai dai iskanci kika ce ba zina ba,kuma in dai iskanci ne,a wannan lokacin ai kowa na ɗan taɓawa,kuma kema zaki iya yi" Kallon shi take baki buɗe "amma baka da hankali Jauro,yanzun ni zaka ce in zan yi iskanci ina iya taɓawa? " Na ga kamar bakida suma,kalli suman kankifa yanda kikasan an sude kwallan mangoro, Ni da naso ace matar da zan aura tana da suma,amma ba komai nayi maneji a haka,sannan zan siya maki wani man suma da naga ana talla a online," Baƙin ciki ne yasa tace"ka fara sai ma kanka sutura tukun na kafin ka yi maganar man kai"tana gama fadar haka ta shige gida cikin jin haushi,tana jin kiranta da yake yi mata da sunan data tsana wato Sumy Baby,ko juyowa ba tayi ba, Tana shiga cikin gida kai tsaye dakin Baba ta shiga da kuka ta tsugunna a gaban shi"Baba ɗan Allah kamin rai ba na son Jauro,bana son na aure shi,dan Allah,na yarda koma waye ka aura min ko da Almajiri ne amma banda Jauro"ta karasa fada tana fashewa da kuka sosai. Kallon ta yayi cikin Alamun rashin wasa yace"nariga na yanke hukunci a kan haka,kuma shi ɗin ba mutumin banza bane ya cika duk wasu sharuɗɗa irin na wanda ya dace aba mutum aure,dan haka ki saka zuciyar ki a inuwa ki kuma hakura dan aure ba fashi,tashi ki ban wuri" "Baba dan Allah" Ta faɗa tana ƙoƙarin dafa ƙafar shi, Wani tsawan ya daka mata"tashi ki ban wuri,mutuniyar banza,ni na haifeki nasan girmanki da burinki har zuwa yanzun,dan haka shi yasa na zaɓa maki wanda naga yafi dacewa dake" Ganin yanda yayi maganar ne yasa da sauri ta tashi ta bar dakin tana kuka, A bakin kofa suka ci karo da Mama wacce take tsaye tana jinsu,dan haka jan hannun ta tayi suka shiga dakin ta, Cikin masifa ta ce "me nace maki?ba nace ki bari zuwa anjima akwai inda zanje ba,wai me yasa Sumayya kike da gajin haƙuri" Sallamar Aminu yaron makociyarsu ne ya dakatar da su,gaida Mama yayi sannan ya miko mata wani bakin leda "Mama gashi wai aba Sumayya inji Jauro" Sai da ta yi kamar ba zata karba ba,sai da ya ƙara mai maita abinda yace sannan ta masa,ba tare da tace mai ko mai ba ya wuce,ganin ya tafi ne yasa ta buɗe ledan, Wani dogon tsaki taja tana wurga ledan ɗakin ta, "Kai wannan mutumin akwai matsiyaci,yanzun Sumayya ya rasa me zai kawo maki sai ledan Burodi sinki biyu,sai kace wasu Fulani,gaskiya dole in tafi wurin wannan malamin dan ba zan iya gaiyar Fulani ba"kallon yar nata tayi,yanda duk tayi wani sanyi," Kinga tashi kije kiyi wanka ki huta,sannan ki cire komai a ranki banda tunani " Jinjina kai tayi"to Mama "sannan ta tashi ta wuce,ruwa ta diba tayi wanka sannan ta koma ɗakin ta,ranar anan ta karya,gabaɗaya ta rasa meke mata daɗi,domin a duk lokacin data tuna shi bata taba ganin dacewarsu sai dai ma ta ƙara ganin wani makusa nashi, Haɗuwar su ta biyu dashi,bayan kusan sati da haɗuwar su a cikin Adaidaita,harma ta manta dashi,amma a duk lokacin data tuna abinda ya mata shida ɗan Adaidaita sai ta tsine mashi, Ranar Mama ce ta aike ta gidan Aunty Aminatta amso mata wasu kaya,ta je ta amso kayan sai tayi tunanin me zai hana ta shiga kasuwa ta siya Ɗan kunni,tun da gidan da kasuwa babu nisa. *🍂JAURO🍂* (MAI ANGUWA) Story & Writing By JIDDARH UMAR 🌟🌙🌙🌙🌙🌙🌙🌟 *🌙✨MOONLIGHT WRITER'S ASSOCIATION🌙✨* https://m.facebook.com/Moonlight-writers-association-109698351308376/ *'''We are the moonlight writers we shine all over the world.''🌍'* ✍️✍️ بِسم الله الرحمن الرحيم ~~~~~~~💞💞~~~~~~~ *Ban yarda wani ko wata su ɗaura min littafi a shafin su ko ya mai da min littafi Audio ba tare da izini na ba* *5* A Babban shagon siyayya ta tsaya wanda naga an rubuta B.S Store,dan bata cika son tayi ta zagaya ba,gara ta tsaya wuri ɗaya kawai ta siya, Shagon babban shago ne sosai wanda ba abinda basu siyarwa, Cikin yanga da jan aji ta shiga shagon wanda ko yaushe baka raba su da jama'a, Layin da ake saida ƴan kunnaye ta nufa,cikin natsuwa ta cire wanda take so,sannan taje wurin biyan kuɗi ta biya aka saka mata a leda, Har ta kusa fita bakin ƙofar shagon sai ji tayi ance "Malama muga ledan dake hannun ki" Dago kai tayi ta kalleshi sannan ta kalli ledan kayan da Aunty Amina ta ɓata ta kaiwa Mama, "Ban gane kaga ledan hannu na ba? " Saboda muna zargin kamar akwai abin mu a ciki" Daga ɗayan ɓangaren taji ance"Sani caje ta da kyau damun ƴan matan yanzun ɓarayi ne,haka jiya daga gaiyatar wata yarinya shan shayi daki na ta sace min DVD da nake kallo dashi" Wani Alhaji dake zaune ne ya tuntsire da dariya"kai Jauro in bada kana ɗan iska me ya kaika gaiyatar mace dakin ka wai shan shayi,dan ka mai da mu ƴan iska" Jin sunan da aka kirashi dashi yasa nan take ta tuna shi,domin ba zata taba mantawa da mutumin da ya mata tayin siyan Condom ba, Shafa kai yayi yana dan dariya "ai wato Alhaji in faɗa maka jiya ne an dan yi sanyi shi yasa na gai yace ta,ban san ashe yarinyar nan barauniya bace,ko yanzun inda zan ganta wlh sai ta biya ni Sidi na" Alhajin ne ya kira sunan yaron daya tsayar da ita"Salisu" Amsawa yayi, "Ko jiya a unguwar ku anyi sanyi? Gabaɗaya kwashewa da dariya sukayi,har da wasu mutanen dake zaune wurin," Ai sai dai in a unguwar su Jauro ne aka yi sanyi dan mu yanzun kan lokacin zafi muke" "Kyale shege ya dai san Me ya ciyo har yake jin sanyi,ai ni yarinyar ma ta burge ni,gara data maka haka" "Ai bani na gaiyace ta ba,kai kuma Salisu kar kayi abinda ke gaban ka,wallahi in ba kayi hankali ba har kai sai ƴan matan garin nan sun maka tunbur sun sace kayan jikin ka,dan haka gara ka caje ta da kyau" Nan ma dariya suka kuma sakawa,in da Alhajin yace"a kwanannan mata na mana sata shi yasa muka kara saka CCTV a ko ina na cikin shagon nan" Wani ne daya fito daga cikin shagon yace"Salisu ina yarinyar da nace ka tare? "Gata nan,yanzun ma nake duba kayan ta" Tsaki mutumin ya ja"wai ne yasa kai a rayuwarka baka yin komai cikin nasuwa ne,ni da ba ita na nuna maka ba,wata farin hijabi,shine zaka tare wannan ka bari Barauniya ta gudu,? Da sauri ya shiga mai da mata kayanta cikin leda "ɗan Allah Madam kiyi haƙuri kuskure ne" Fisge ledan dake hannun shi tayi "ba ni da lokacin mahaukaci irin ka" Taku biyu tayi ta tsaya a gabansu,idon ta yayi ja,wanda har ya tara ruwan hawaye,wannan wani irin tozarci ne,a gaban mutane,ai ko bata ɗauka ba sun bata mata suna, "In Allah ya yarda sai ƴan mata sun sace ka sannan suyi gunduwa gunduwa da kai su sai da naman ka"tana gama faɗar haka ta fita shagon tare da Addu'ar kar Allah ya ƙara haɗa ta da wannan mutumin domin ko yaushe hadurwata dashi baya tamo mata Alkhairi,. Kallon shi sukayi yanda ya sake baki yana kallon ta,sai kuma suka kwashe da dariya,wanda Alhajin tsabar dariya har yana dukawa tare da rike ciki, Kallon su yayi"To me na mata" "Me yasa baka tambaye ta" Ƙara kallon hanyar da rabi yayi "naga dai wannan karon ba da ita nayi magana ba,kodan nace yan mata take jin haushi na" "Kama santa kenan ko Jauro" "Eh to na dai taɓa mata tayin ko zata siya Condon a cikin Adaidaita wancan satin" Duk zaro ido sukayi suna haɗa baki"tallan Condon,wannan budurwar? Salisu ne ya ce"lallai Jauro baka dibo da sanyi ba,yanzun ka taba ganin in da aka ma budurwa tallan Condon ko da kuwa ƴar iska ce" Bata fuska yayi "yo ni ba taimaka mata nace zan yi ba,kuma ai sa'a ce kuma su nake taimako" "To wai in banda hauka ma irin naka me na sai da Condon? " Nifa Dila ne,tunda bama da kamfanin nan Nigeria nake aiki ba,daga ƙasar Moroko ake kawomin Condon wanda da amincewar manyan kasarnar,da hukumar Lafiya na WHO, Kuma an yi hakan ne saboda taimakon jama'a" "Ta ya hakan ya zama taimakon jama'a" Gyara zama yayi yana fasa ledan ruwa dake gabanshi ya zuke,"yanzun zamani ne na Family Planning da mata ke yi domin tsayar da haihuwa,wasu su saka na hannu,wasu kwayoyi na haɗiya,wasu Allurai,wanda dukkan su babu wanda bai da matsala,kaga kamar na kwaya,shi taruwa yake a mahaifa baya narkewa,karshe ya bata masu mahaifa a kai ga cirewa,Allah ya tsare, Shi kuma Allura ko dai yasa mace ta shanza kamanni ta hanyar hurata,ko kuma ya sakar mata da jini,ko jinin yata wasa,gadai shinan,kaga wannan duk cutarwa ne, Sai kuma wata hanya wanda ba ko wasu ma'aurata ne suke iya yin shiba,kuma shine hanya mafi sauƙi,wanda baya cutarwa,kuma Addini ya yarda dashi,malamai kuma sun tabbatar da babu matsala idan mutum yabi wannan hanyar,wanda ita ce Withdrawal Method (Pulling out) ba zaka zuba komai ba a jikin matarka,sai dai ka juye a waje,wasu kuma basu sanin sanda suke juyewa,to saboda haka aka yake da kyau amfani da Condom,ko ga ma'aurata wannan ba laifi bane, Kaga wasu da yawa da auren su amma sai su haifi Unwanted child,ya'yan da ba'a so,wanda iyayensu basu shirya haihuwar su ba,kaji uwa na cewa ai wlh banma shirya haihuwa ba na haife shi,ko kuma iyaye su dinga jin haushin ya'ya saboda sun haifesu alokacin da basu shirya haihuwa ba,ko kuma ɗawainiya sun masu yawa,hakan sai ya ja su dinga hantaran ya'yan kamar basu suka haife su ba, Su kuma yan mata,saboda gudun Sexual Transmitted Infection,kuma ni dila ne ba wa kananan abu ba,shi yasa na mata tallah,ashe taji haushi na" "To wallahi kayi a hankali in ba haka ba wata rana sai mata sun maka duka,ko kuma su daddatsaka kamar yanda waccen Budurwar taka ta faɗa" Alhajin ya karasa fada yana kwashewa da dariya. Tsaki yaja "ni kam na wuce dan yau Ruga nake son na kwana" Ajiyar zuciya ta sake tana zamewa ta kwanta,wanda daganan barci ya kwashe ta, Koda ta farka har ƙarfe goma sha ɗaya na safe tayi,dan haka kuskure baki tayi tare wanke fuska,ta fito ɗan daura girkin rana, Kallon tsakar gidan nasu tayi yanda yayi shiru,"Aisha ina Mama"ta tambaye yarinyar dake zaune kofar daki tana wasa da kwankwalati, "Mama ta fita,tace idan kin tashi nace ki daura girki sannan ta tafi gidan Matar Kansila" Shiru tayi tana tunani,kenan Mama ta tafi,Allah dai yasa naji kyakkyawar labari... *🍂JAURO🍂* (MAI ANGUWA) Story & Writing By JIDDARH UMAR 🌟🌙🌙🌙🌙🌙🌙🌟 *🌙✨MOONLIGHT WRITER'S ASSOCIATION🌙✨* https://m.facebook.com/Moonlight-writers-association-109698351308376/ *'''We are the moonlight writers we shine all over the world.''🌍'* ✍️✍️ بِسم الله الرحمن الرحيم ~~~~~~~💞💞~~~~~~~ *Ban yarda wani ko wata su saka min littafi a shafin su ko su mai da min littafi Audio ba tare da izini na ba* *6* Yana barin ƙofar din su bakin titi ya nufa,dama ranar a cikin gari ya kwana shi yasa yace bari yazo ya dubata, Yana tare abin hawa yace ya kaishi Cancaga,suna zuwa ya sauka,daga bayan shi yaji ance"Jauro ina zuwa? Juyowa yayi,ganin wanda yayi magana ne yasa yayi murmushi,cikin harshen Fulatanci yace mashi"gida zani" "Oh bamu gaisa ba,barka da safiya ka tashi lafiya" Yana hawa mashin dinshi yace "lafiya klau ya iyalan naka" A lokacin ya tada mashin din yana amsawa,a haka suke tafiya suna dan taɓa hira kasancewar Musa kanin abokin shi ne,da Cancaga da rugarsu bai da nisa sosai dan ana iya shigar da kai a naira Dari da ishiri,a yanzun ma kenan da mai yayi tsada, Sun yi tafi wanda aƙalla bai wuce tafiyar mintina goma ba su karasa cikin rigar ya kalle Musa yana dafashi a kafaɗa "Musa" Ya kira sunan shi. "Na'am Jauro" "Ina ga ka maida ni kawai Cancaga ko kuma ka sauke ni na koma da ƙafa" Ɗan juyowa yayi "lafiya kuwa bayan mun kusa karasawa" "Lafiya glau,kawai dai nayi mantuwa ne,a kwai maganin dana siyo ma dabbobi kuma na manta dashi" "To ka bari kaje ka huta mana ko zuwa anjima sai ka koma ka ɗauko" "Na Baffa Bube ne" Da sauri yace"A'a to bari na mai da kai kuwa"nan take ya juya akalar mashin ɗin,ya mai da shi in da ya dauko shi,sallamah suka yi ya kuma hawa wani Adaidaita ya dawo dashi cikin gari inda yake zaune yake haya, Harya ɗauki ledan maganin shanayen sai ga kira ya shigo mashi a kan ana niman shi a wurin aiki da sauri, Ba yanda ya iya dole ya mai da maganin ya ajiye ya tafi wurin aiki da zummar in ya dawo komai dare a ruga zai kwana saboda ya kai ma Baffa Bube maganin shanayen shi kamin ya tsine mashi. A ranar bashi ya dawo ba sai ƙarfe takwas na dare,yana shigowa wanka yayi,yana fitowa ya dauki wayarshi dake ƙara tun yana bayi,ganin me kira ne yasa ya ɗauka da sauri,kafin yayi sallamah yaji yace"Jauro kana ina" "Ina gida,lafiya na jika haka? " Wani gida? "Cikin gari" "Kana jina" "Eh,amma lafiya Adamu? " Ba lafiya ba,duk inda kake karka kuskura ka shigo Ruga,domin dazu da ko Sallar Isha'i ba'a idar ba,aka shiga gidansu Baffa Sanda shida matarshi aka dauke su,sun kuma harbi Yaya Audu yanzun haka ana shirin kawoshi Asibiti dan haka kar kazo" Gabaɗaya duk ya ruɗe "me kake nufi da an ɗauke su,su waye suka ɗauke su? " Kidnapping dinsu aka yi,dan haka sai ka kiyaye Allah ma ya taimaka baka kusa" Shiru yayi yayin da zuciyar shi ke zafi,sai kuma yace"suwa suka aita wannan aikin" "Baka buƙatar amsa domin ka sani,kuma kasan abinda ya faru da Jabbi kwanaki uku da suka wuce,tayu tasu hanyar daukar fansan kenan" Dafe kai yayi "ya Allahu,shi kenan na gode Audu,insha Allah zan kiyaye" "Yauwa sai kaji ni kuma"nan suka sauke wayar, Komawa yayi kan gado ragaf ya faɗi,yana lumshe ido, A gaskiya ƙaddarar shi mai ƙarfi ce tunda Allah ya ƙaddara haihuwar shi a cikin Ahalin JAURO waɗanda suka kasance wasu irin hallittu da Ubangiji ne kawai yasan manufarsa na Halittar, Su ba dabbobi ba ne amma kuma zuciyar su bana mutane ba ne, Idan aka ce Ahalin JAURO indai ana maganar Dukiya na Dabbobi to Allah ya basu wannan Arzikin, Baƙin ciki,harsada,da kyashi,wanda har yakai matakin da zasu iya hallaka junansu, Ya taso acikin wata iri yar rayuwa mai cike da kalubale,tsana,tsangwama,rashin madafa,da kuma rugujewar buri,ya zamo ɗan marayan Dawisu a cikin mugun dawa,wanda yake ɗauke da mugayen namomin daji masu matukar hatsari da yunwa,wanda a ko wani lokaci suna iya kawo ma wannan Marayar Dawisu farmaki,ko nace sun sha kawo mashi Farkami inda Ubangiji ne kawai yake kareshi da kariyar sa,ya kuma saka shi acikin mutane masu tsayin rai acikin wannan dawar,yasa ya kasance a cikin zababbu bayan doguwar gwogarmaya. *Asalin Ahalin* Asalin Kakanshi shine Abdul Aziz,wanda ya kasance Ba'adare Bafullatani ne,wanda ya tara dukiya na Dabbobi daya gada a wurin iyayenshi, Yana zaune ne a can wani ƙauye tare da Yayanshi guda biyar,maza uku mata biyu,, Danshi na farko shine,Baffa Sanda,sai Baffa Dottiya,sai Baffa Bube,sannan gwogo Badejo,da kuma gwogo Halira, Ada iyayensu ma'abota tashi ne daga wannan garin zuwa wannan kafin su tsaya a gari daya,wannan yasa gabaɗaya yaran nasu ba abinda suka sani dangane da Addini daya wuce noma da kiyo, Haka ma iyayensu, A tare da yaran babu wani shakuwa ko nuna soyayya irin ta ƴan uwantaka,babu ragi ko kadan a tsakanin su,idan daya daga cikin su yama ɗan uwanshi laifi to uwarsu zata ce lallai sai ɗayan ya rama dan yana dan wanshi bai isa ya masa yaki ramawa ba,da haka tarbiyarsu ta taso babu ragi a tsakanin su,kamar yanda babu sabo ko shakuwa a tsakani, Ana cikin haka ne Allah ya fara dauke Abdul Aziz wanda suka fi kira da JAURO,daga baya ne suka tashi daga wurin da suke suka yanka tafkeken fili a nan Cancaga,aka kuma raba masu Gabon su kamar yanda suka buƙata, Kowanne ya samu shanaye da suka kusa tasanma rabin garke a cikin su,Matan ma aka ba kowacce nata tayi gidan mijinta dashi,domin suna shekara goma sha biyu JAURO ya auran da kowacce, Baffa Sanda ne yafa yin aure inda da ya aure wata Bafullatana mai suna Kande,sai da yayi haihuwa daya kafin Baffa Dottiya wanda yake Mahaifi a wurin Jauro, Ada kafin auren Baffa Bube suna dan lallaba yanayin zaman nasu,duk da ba kasafai suke kula da lamarin juna ba, amma lamarin nasu da ɗan sauki, Domin Kande matar Baffa Sanda tana da Yara Biyu,daya ana kiranshi da Dotti,daya kuma Yabbale, Sai matar Baffa Dottiya wacce a lokacin ɗan ta daya mai suna Abdulaziz suna mashi lakabi da sunan kakanshi Jauro, Tun daga lokacin da Baffa Bube ya auri matarsa mai suna Jabbi,ta tako cikin gidan da suna matar gidan,tun daga wannan rana duk wani farin ciki da ya ɗanyi saura a cin gidan ya karasa tarwatsewa,duk wani kwanciyar hankali dake gidan ta karasa koranshi,ta maida gidan filin yaƙi da farauta,ta hana kowa zaman lafiya ciki kuwa har da ita karan kanta,ta kara zama wata muguwar shaidaniya.............. *🍂JAURO🍂* (MAI ANGUWA) Story & Writing By JIDDARH UMAR 🌟🌙🌙🌙🌙🌙🌙🌟 *🌙✨MOONLIGHT WRITER'S ASSOCIATION🌙✨* https://m.facebook.com/Moonlight-writers-association-109698351308376/ *'''We are the moonlight writers we shine all over the world.''🌍'* ✍️✍️ بِسم الله الرحمن الرحيم ~~~~~~~💞💞~~~~~~~ *Ban yarda wani ko wata su saka min littafi a shafin su ko su mai da min littafi Audio ba tare da izini na ba* *7* Zuwan Binta da kwana uku ta haddasa fitinar da tasaka sai da aka raba babban gidan da suke zaune kashi uku,domin kuwa a ranar ne ta je ta samu Baba Mari,mahaifiyarsu da kuka cewar wai tana cikin wanka sai taji ana lekenta tun da tazo,to shine yau Allah ya bata sa'a ta kama wanda yake leken ta,sai dai taji tsoro da ganin wanda bata yi zata ba,wato yayan mijinta Sanda,gaskiya ba zata iya zama ba zata koma gidan su ne ta fada tana kara fashewa da kuka, Hankalin tsohuwa ya tashi,ranta yayi mugun bace,domin kuwa a garesu abin kunya ne babba ace daga aure amarya ta gudu,kuma dalelin kasancewa wai sai aji yayan mijinta ke lekenta idan tana wanka,dan haka cikin gaggawa tace maza a nimo mata Sanda yanzun nan, Haka kuwa aka yi,yana zuwa ya duka a gabanta yana gaishe ta da harsher Fullanci,kin amsa shi tayi,wanda hakan ba ƙaramin mamaki ya bashi ba,dan yasan koda safe lafiya suka rabu, "Inna lafiya" Ya tambaye ta. Cikin masifa tace"wani irin abin kunya kake kokarin janyowa zuri'a ta,yanzun saboda rashin gode Allah matarka bata isheka ba har sai ka haɗa da na dan uwanka,wacce ko kwana uku bata cika ba a gidan nan,dama haka halinka yake bamu saniba sai yanzun Allah ya toni Asirin ka " Duk wannan maganganun da take yi kanshi ba ƙaramin kullewa yayi ba,to me kuma ya haɗa shi da matar dan uwan shi,wacce bai ma ko gama tantance fuskarta ba, Dago kai yayi da zummar yi mata tambaya,sai dai ji yayi an shakoshi anyi wurgi dashi a tsakar gida,an kuma bishi da sanda ana ƙoƙarin rafka mashi akai,wanda da badan yayi sauri cikin zafin nama ya kauce ba daya raba mashi kai biyu, Cikin mamaki yake kallon dan uwan shi Bube, "Me haka Bube,me na maka ne haka " Har wani huci yake fitarwa na bacin rai yana nuna ɗan uwan nashi"yanzun ni zakaci amana Sanda,ni zakaci amana ka dinga labewa kana kallon tsiraicin mata na saboda baka tsoron Allah,to yau sai na ga bayan ka"ya faɗa a zafafe yana nufarshi, Oh sai yanzun ya fahimci inda maganar ta dusa,shima nan take ranshi ya motsa,ya kalle dakin da Inna ke zaune tana bantalar goronta hankali kwance,yayin da Binta ke kofar inna tana kallon rigimar da suke yi, Sai matarshi Kande wacce shigowar ta kenan daga dibo ma dabbobi harawa wadanda ba'a fitar dasu kiyoba na mijinta, Ganin abinda ke faruwa da kuma jin furucin Bube yasa cikin kidima ta zubar da abin dake hannunta tanufe dakin inna da gudu tana kuwa,tsugunnawa tayi a gaban ta "dan Allah inna ki shiga tsakani ki raba wannan fitinar" Ture ta tayi"ɗan Allah matsa can,ke yazun ba abin kiyi Allah wadai bane da Abinda mijinki ya aikata,matar dan uwansa da ya kalla," Cikin kuka take girgiza kai"wallahi ba halinsa bane,ba halin Sanda bane,na tabbata ba zai aikata haka ba" "Ka jimin munafukar yarinya,har ni zaki faɗa ma halin ɗa na,yaron dana raine shi tun kafin ki haɗu dashi,,to sai kije kiyi duk yanda zaki yi dasu ni dai bani daddakawa daga nan"ta faɗa da masifa, Cikin tashin hankali ta nufe inda Binta ke zaune tana kuka ta rike hannunta " Dan Allah Binta ki faɗa gaskiya domin nasan hakan ba zai taba faruwa ba,na yarda da mijina na kuma yarda da halinshi," Ture hannun ta dake saman nata tayi"kenan kina tunanin karya na ma mijin ki ko me,to bari kiji,ko ki yarda ko karki yarda abinda ya aikata min kenan,kuma sai miji na yau daukar min fansa" Daga bayanta taji ance "fansar me za a ɗaukar maki" Duk juyawa suka yi,suna kallon ta,gabaɗaya ta kere su tsayi da girman jiki,macce wacce take a tsaye,ga kazar_kazar,wato Halima kenan matar Baffa Dottiya, Kallon cikin idanun Jebbi tayi,tana nunata da yatsa"ke daga ganin waɗannan idanun naki akwai munafurci da makirci a tare dasu,da yaushe mutumin da baya zama gida ya leka ki kina wanka" Cikin tashe rashin kunya da nuna eh ba tsoronki nake ba tace"idan bai lekaba sai akayi ya,ko zaki shigar mashi ne,dan ni ban shigo gidannan da tsoron kowa ba"ta faɗa tana nunata da yatsa, Ba zato ba tsammani sai ji tayi an kama yatsan an riƙe,sai kuma raji an juya,kafin ta fahimci me take kokarin yi sai jin wani azaba tayi ya ratsa ƙwaƙwalwar ta ya sauko saman ɗan yasan daya bada sautin Kas sannan ta sake, Dago hannun tayi tana kallon yanda yatsar ya kwanta yana lilo,alamun kashin dake rike shi ya ƙarfe, Wani ihu ta zunduma tana faduwa kasa tana birgima tare da rike hannun ta, Jin ihun matar tashi ne ya saka da sauri yayi jifa da sandar dake hannun shi wanda ye kaiwa Baffa Sanda hari dashi,shi kuma yana goshewa domin ba shida abin da zai kare kanshi,har kuma ya samu damar samun shi a hannun wanda wurin tuni ya kumbura, Dago ta yayi yana riƙe hannun tare da tambayarta lafiya,cikin kuka da ihun azaba take nuna mashi Halima dake tsaye tana masu kallon uku saura kwata"wannan maiyar ce ta karya min hannun,kalla ka gani,waiyo shi kenan zan zama mai yatsu huɗu kenan" Da sauri Inna Mari ta fito,"ke Halima me ta maki kika karya ma yar mutane hannu" Sai da ta harari gefe tukunna kafin ta kalli Inna ido cikin ido tace"yatsa ta nuna min,ni kuma naje sauke mata sai aka samu akasi domin ashe kashinta bai da kwari,kinsan Inna ni ban cika son ana nuna min yatsa ba," Ganin duk sun tsaya suna kallon ta ne yasa ta kuma cewa"nifa ba da gangan nayi ba,Inna kawo hannun ki in nuna maki yanda na mata,zaki tabbatar da kashinta ne bai da kwari" Da sauri inna ta mai da hannun ta baya ta juya tana korarin shiga daki tare da faɗin,"dama Awala hakkillo,"ta fada tana karasa shigewa daki tare da sauke labulen dakin ta,dan sarai ta san halin Halima ba cikakken hankali gare ta ba,dan tana tare da mugun iskokai idan ka yi rashin sa'a kuna cikin hayaniya da ita suka tashi to kashiga uku,domin cutar rabkuwa suke saka mata,wato idan ta rike mutum zata ringa rabkashi da kasa ne yanda kasan ana bugun fulawa,kuma ta taba rabka inna Mari wacce sai da aka mata ɗaurin haƙarƙari shi yasa duk cikin sirikanta tafi shakkar Halima.... *Na yi kuskure a sunan matar Baffa Bube mai suna Jabbi,yanzun sunan ta Binta* *🍂JAURO🍂* (MAI ANGUWA) Story & Writing By JIDDARH UMAR 🌟🌙🌙🌙🌙🌙🌙🌟 *🌙✨MOONLIGHT WRITER'S ASSOCIATION🌙✨* https://m.facebook.com/Moonlight-writers-association-109698351308376/ *'''We are the moonlight writers we shine all over the world.''🌍'* ✍️✍️ بِسم الله الرحمن الرحيم ~~~~~~~💞💞~~~~~~~ *Ban yarda wani ko wata su saka min littafi a shafin su ko su mai da min littafi Audio ba tare da izini na ba* *8* Ganin irin kallon da take masu ne yasa bai ce mata komai ba ya kama hannun matar shi dake ihun hannunta ya taimaka mata ta mike sannan suka bar wurin, Da sauri Kande ta karasa wurin da mijinta ke tsaye tana rike hannun shi, Daga inda take tsaye tana kallon su amma bata San me suke fada ba,dan haka kaɗa kai kawai tayi ta koma dakin ta, Sai bayan Sallar La'asar wuraren biyar Baffa Dottiya ya dawo,shine inna ta aika Yabbale ɗan gidan Baffa Sanda da ya kira mata iyayen shi maza duka tana son ganin su, Haka kuwa aka yi duk suka halarta kiranta,sai dai tsakanin Sanda da Bube ba wanda ya zauna kusa da ɗan uwan shi,kuma hakan be dame ta ba,illa daurawa da tayi da faɗin "nasa an kira kune dan na sanar daku lallai duk inda za ku nimo masu gini ku nimo,domin a gobe nake so a raba wannan gidan kashi uku ai ma ko wanne katanga,dan ba zan iya da wannan abin kunyar da kuke ƙoƙarin jawo min ba, gara a raba ya zamana ba mai shiga ɓangaren ɗan uwan shi" "Yauwa Inna,wannan hukuncin naki yayi,dan gaskiya zama gida daya da kwartaye hatsari ne,dama kuma ko baki faɗi haka ba inada niyar aikatawa" Baffa Dottiya ne da bai gane meke faruwa ba yace"wani irin Kwarto,sannan muna zaune lafiya ne yakawo batun rabon gida?ya tambaya yana kallon su, Nan Inna ta kwashe komai ta sanar masa,ai kuwa mai zai yi banda dariya har yana tafawa,nuna Sanda yayi da hannu"yanzun kai ka rasa wacce zaka tsaya leke sai wannan mai kama da Kurbirgar(Muciyar tuwo)" Nan take ran Baffa Bube ya ɓaci jin sunan daya kira matar shi, Cikin jin haushi yace "ai gara nawa matar suffar muciya gare ta,ko ba komai mata ke rike muciya ba maza ba,kaga kenan ko tanan tana da suffar mata, akan matarka da take a tsaye kamar Garii (namijin bigimi),kuma wannan munafikin babu ni babu shi har abada kai har ranar tashin ƙiyama,ko zuri'a ta ban yarda ka kirasu da ya'yan ka ba,kamar yanda Ya'yan ka ba ya'yana bane har tashin duniya,Inna ki zama shaida "Sai me dan kace haka,aikin banza,Allah na gode maka daka fara bani yaya baka yini juyaba,da na kashe kai na dan bakin ciki,kuma ko baka faɗa haka ba,dole haka zai faru saboda wannan shedaniyar da ka Aura,kuma ina mai tabbatar maka kai da kwanciyar hankalin iyali sai dai a lahira in ana yi kayi,dan na lura baka cikin masu rabo"yana gama fadar haka yaja dogon tsaki ba tare daya ce masu komai ba ya mike tsaye yana barin ɗakin,domin bazai lamince tozarci irin na yan uwan shi ba, Ganin ya bar dakin ne yasa kowannen su ya tashi ya bar dakin cikin jin haushi ba tare da ko wanne su ya ma tsohuwar da ke zaune magana ba,kamar yanda ita ma bata ce masu kuci kanku ba. Washegari da safe ko gama wayewa gari bai yi ba,sai gashi masu aiki sun zo wadanda Baffa Sanda ne da kanshi ya gaiyato su domin su kangemai shiyanshi dana matarshi,sannan yasa a kara buga masu Bukka, A taikaice dai a wannan gidan rana bata faɗi ba sai da aka kange waɗannan shiyoyin guda uku, Hakan ne yasa gidan aka ɗan samu kwanciyar hankali na kwana biyu,domin kowa na shiyan shi, A tsakanin kwana biyun nan kuwa,sam Baffa Sanda ya hana Yayanshi shiga shiyan sauran ƙannen nasa,sai dai shi jauro yana shiga wurin yara ƴan uwan shi,kun dai san yanda yara suke, Ana cikin haka ne Baffa Dottiya ya tattara kayansa da dabbobin sa wai zai tafi cirani, A cikin su ba wanda ya damu da hakan domin su a al'adar su ba wani abu bane, Cikin taimakon Allah kuwa suka bar gida shida matar sa wanda a lokacin Jauro yanada shikara biyu da rabi, A kwana a tashi babu wuya a wurin Allah dan wasa_wasa sai da Baffa Dottiya ya kwashe shigaka hudu a wurin yawon shi na kiyo daga nan garin zuwa nan garin kafin su waiwaye gida, tare da tarin Alkhairai domin kuwa a lokacin dabbobin shi na shanaye kaɗai sun tasarma garke biyu da yan kai,kamar yanda tumakai wato raguna sunkai garke daya,ya nada yara wadan da suke binshi kusan su huɗu,yana biyan su domin su tayashi kula da dabbobin shi,sai dai shi ya rigasu isowa gida dan su suna hanya,saboda rashin lafiyar matarshi shi yasa ya fara wutowa gada, wanda a lokacin abubuwa da yawa sun faru,kuma suna kan faruwa,domin kuwa Matar Baffa Bube a lokacin yaranta biyu,kuma tana dauke da cikin na uku, Ko da suka dawo a shiyansu na da suka sauka kuma ita ma Halima lokacin cikinta na da wata takwas,wanda yake matukar bata wahala,kusan ko yaushe a kwance take ba lafiya, A washegarin ranar da suka dawo ne taja hannun ɗanta suka shiga shiyan Inna Mari wacce ke shiya daya da Baffa Bube,domin kuwa duk cikin ya'yan ta tafi son shi, A hankali suke tayifa har suka shiga shiyan wanda tun daga bakin kofar zaka fara jin hayaniya na tashin hankalin da ake yi, Duk da hayaniyar da take ji hakan bai sa ta fasa shiga ba, Sai ma kallon ɗanta da tayi "Har yanzun iyayen ka sunki suyi hankali" Shima baice komai ba sai kallon ta da yayi, Da sallamah ta shiga ɗakin Inna wacce take zaune tana sauraren bayanin da Binta ke yi "wallahi ba zan yarda ba,haka kurin ban haifarwa wata katowa ɗa na ba danta dinga jibgarshi ba,ba zan lamunta ba,haka jiya tsabar mugunta ina kallon ta data shigo kawo maki tuwo ta tunkuɗe Bakari,sai da kanshi ya bugu da tukunyar miya,na dai yi shiru ne kawai na kyaleta domin kar ka yi magana ace bakada kara akan dan fari,shi ne fa In faɗa maki Inna yau tana shigowa wai yaron nan Ɗan Fodiyo yazo da gudu cikin rashin sani ya buge ta,baƙi ga yanda ta daddage ta zuba mai Mari ba iya karfinta dan rashin imani,to wallahi ba zan yarda ba,ko dai adau min mataki ko kuma na dau ka da kaina"ta fada tana jijjiga jiki, Ita ko Kande sai cewa tayi "kin daɗe ba ki dauki matakin da kanki ba,an gaya maki tsoronki nake yi,in banda rashin Albarka irin naki ke kika turo Ɗan Fodiyo ya zo ya bangajeni,yaro ina mai magana saboda rashin tarbiya sai cewa yayi ni ba ɗan ki bane da zaki min magana,har da hararata,ni tsaran shi ne" Inna ce tace"to ba gaskiya ya faɗa ba Kande,ke uwar shi ce,ke ba uwarshi ɓace dan yaro ya faɗi gaskiya kuma sai kiji haushi,ke dai kawai ki fada wani dalili ne a kasa"kallon Binta tayi wacce take cika tana batsewa"ke ni ban iyawa da jarabarku idan ki nada yanda zakiyi da ita kiyi,me na cewa in dauki mataki,ku tafi na sallame ku ku bani wuri"ta fada tana nuna masu hanya, Kande ce ta fara fita tana faɗin "sai ki yi duk abin da zakiyi domin dai nasan nafi karfin duka a wurin ki... Kafin ta ankara sai ji tayi an wurgo mata marfin tukunya wanda bai tsaya a ko'ina ba sai saman goshin ta,nan take kuwa jini ya ɓalle,dafe wurin tayi tana kallon Binta wacce ke huci, Kutmar uba,ai kuwa ba tayi katsa a guiwa ba tayi cikin Binta wanda nan take kokawa mai ƙarfi ya shiga tsakanin su, Babu imani kuwa Kande ta shiga rusa mata kulli a ciki,wanda yake bai wuce wata uku ba,duka kuwa take har saida ta kaita kwance, Dakin Inna kuwa duk abinda suke tana jin su sai cewa da tayi " Tsinannu sai ku kashe kan ku ai" Ita dai da kyar ta mike tasan ko taje ba iya rabasu za tayi ba,domin ba daɗin jikinta take ji ba, "Inna barka da safiya," "Ke raba ni da barka samun waɗannan tsinannu ba zasu bari na wayi gari lafiya ba" "Inna bari in duba ko zan samu makota su zo su raba wannan faɗar" Bata ce mata komai ba sai tabe baki da tayi, Ta gefen su ta raba ita da ɗan ta suka fita,domin duk da tana kallon yanda jini ke diga daga goshin Kande kamar yanda jini ke gangara daga ƙasan Binta, Bata iya sauri gashi kuma yanayin gidan fulani,daya can daya can,basu gida kusa da juna,dan haka kallon ɗan ta tayi"Jauro kayi gudu kaje ka kira duk wanda ka ci karo da shi " "To inna na" Da gudu kuwa yaro ya fita,cikin sa'a kuwa ya haɗu da matan Fulani su biyu suna ƙoƙarin shiga gida,rike hannun daya yayi cikin yaren fullanci yace,kuzo gidanmu Inna na tace in kira ko waye saboda ana faɗa, Jin abinda yaron yace ne yasa suka bi bayan shi,ita ta masu jagora har shiyan Binta wanda zuwa lokacin duk sun jigata..... *🍂JAURO🍂* (MAI ANGUWA) Story & Writing By JIDDARH UMAR 🌟🌙🌙🌙🌙🌙🌙🌟 *🌙✨MOONLIGHT WRITER'S ASSOCIATION🌙✨* https://m.facebook.com/Moonlight-writers-association-109698351308376/ *'''We are the moonlight writers we shine all over the world.''🌍'* ✍️✍️ بِسم الله الرحمن الرحيم ~~~~~~~💞💞~~~~~~~ *Ban yarda wani ko wata su saka min littafi a shafin su ko su mai da min littafi Audio ba tare da izini na ba* *9* Ko da suka isa tuni Binta ta daɗe da suma sakamakon jinin da ya ɓalle mata, Hankali su ya tashi sosai dan haka daya daga cikin matan ne tace bari ta je tama mazajen su magana tunda sunada mashin sai azo a tafi dasu Asibiti, Duk amincewa suka yi da shawarta,dan haka da gudu tayi gida ta faɗa masu, Da taimakon waɗannan matan ne aka ɗaura su a mashin aka yi asibitin dasu,sai dai Halima bata bisu ba,dan cewa tayi ita kam bata iya hawa mashin dan haka su tafi kawai, A ranar dai ita Kande ta dawo,ita ko Binta sai da tayi kwana uku a Asibitin sai da tasha karin jini leda biyu,sannan ga ciki ya zube, A kwana na uku ne da suka dawo Goggo Badejo ta zo,ɗan ita ma sau daya ta leka Asibitin, Kallon Inna tayi tace "Inna ya kamata muje ki gaida Binta da jiki tunda ta dawo" Kallan uku saura tayi mata"in gaida ita na me,ni na aiketa da zan mata sannu,ai da mutuwa tayi ni ba abinda ya dame ni da ta mutu Ɗa na aure zai ƙara,kuma ko yanzun tayi ta gama aure zansa yayi " Bata ce mata komai ba ta tashi ta fita abinda,itama bata shiga dakin Binta ba sai tayi shiyan Baffa Dottiya wurin Halima, Tun daga ranar da ya kira waɗannan Fulanin a gidansu shi kenan ya samu wurin zuwa wasa dan a gidan sunada yara sosai, A cikin su a kwai wanda ake kira da Moha yaron zai kai shekara goma,yana da son karatu sosai,yana zuwa makarantar Boko dan alokacin yana primary four ne, Tunda yaga yana karatu shikenan abun ya shiga ranshi ya manne mashi duk inda yayi yana like dashi wai sai ya koya mashi, Washegari da safe kuwa tunda safe kuwa ya tashi ya tafi gidan su Moha,tare suka karya,sai da zai tafi makaranta labari ya canja,domin kuwa da kuka da ihu da komai aka raba su, Ko da ya dawo gida ba karamin na ci ya dinga ma Baffa da Halima ba akan su bar shi ya dinga bin Moha amma sun ƙi amincewa, Ko da Goggo Badejo ta shigo dakin yana kwance yana barci amma sai faman sauke ajiyar zuciya yake, Kallon shi tayi ta kalli Halima dake zaune tana dama fura, Zama tayi a kusa da ita tana nuna shi"shi kuma wannan ne akai masa da saffafen nen yake faman sauke a jiyar zuciya? Ita ma kallon shi tayi tana tabe baki"kwana biyun nan rigima yake ji wai sai an saka shi makarantar Bokoko,ganin wani ɗan mikotan mu na zuwa" "Oh Boko,ai makaranta ce,kuma bashi da wata illa,kinga ko mu a wurin mu yara na zuwa sosai,ni ma bana zan saka Muntari,kin ga ma shi yana so me zai sa kuma hana shi,kawai ku bar shi ya je" Kallon ta tayi"to sai dai kima ubansa magana dan ni babu ruwa na"ta faɗa tana mika mata lafiyayyen kwaryan kindirmon data dama. "A'a bana Jauro bane? " Ke dai karɓi bari na dama mashi wani" Amsa tayi,shi yasa duk cikin gidan tafi shiri da ita saboda ba tada rowa"an jima zan ma Dottiya magana gobe da kaina zan kai shi makarantar tunda yana so" Da haka dai suka ci gaba da hira, Haka kuma akayi,kamar yanda ta faɗa haka tayi ma Dottiya magana,kuma ya amince,tare da faɗin,ai idan ya gaji da kanshi zai bar zuwa, Washegari kuwa da taimakon Moha ta je makaranta su dake Chancaga makarantar Government ne,ta kammala mai komai inda a lokacin kyauta aka bashi kayan makaranta harda takardu,sannan aka nuna mashi ajin shi aji Daya wato Primary one dan a makarantar Government ba suyin Nursery class,wannan kenan. Ta ɓangaren Baffa Dottiya kuwa tambayar shi Baffa Bube yayi a lokacin suna dakin Inna Mari da safe sun haɗu wurin gaishe ta "ni ko Dottiya yanzun dabbobin ka sunkai guda nawa? Kallon ɗan uwan nashi yayi" Garke biyu da yan kai,sai tumakai" Duk kallon mamaki suke mai harda Inna "yanzun dabbobin ka har sun kai garke biyu bancin tumakai? " Eh" "Amma shine nawa dabbobin yanzun da suka rage ko garke daya basu kai ba,ko dai kana bin ta wata hanyar ne Dottiya" "Ah to faɗa mashi,ni dai duk wanda ya dauko fitinar shi ta tsaya can a kan shi" Cawar Inna, Kallon su yake cikin mamaki"yanzun ni zaku ma irin wannan zargin kuma har da ke Inna,haba sai kace bake kika haife ni ba" "Yo ko ni na haife ka ai kullun cikin canza hali kuke,balle kai da kayi sheka hudu baka gida" Kafin ma ya samu damar mata magana sai ji yayi Bube yace "To ni dai ina rokan ka bani kiyon iri koda shanaye guda ishirin ne" Kallon mamaki yake mai "in baka fa kiyo kace,bancin naka wanda kake dasu" "Kwarai kuwa ai kiyo nace ba kwayta ba" "To ba zan iya ba" Ya faɗa yana mikewa, Inna ce tace"kai ko ai kyauta ma kana iya ba dan uwan ka" "Inna ki ƙyale shi yaje ya gani in dai ni ya ma haka" Bai kula suba ya juya ya wuce yana kananun magana,dan bai zaci haka daga ɗan uwan shi ba, A washegarin ranar ne Halima ta tashi da matsanancin ciyon ciki,wanda tun tana daukar abin da wasa har ya fara cin karfinta,gashi Dottiya ya fita cikin gari,shi kuma Jauro ya tafi makaranta, Abu kamar wasa duk maganin da take tunanin zai taimaka mata tasha amma abu kamar ƙaruwa yake,ji take cikin jikinta ya dawo mata zuciya ya tsaya, Tun tana iya tashi har yakai ta fara fita haiyacinta domin kuwa jini ne ya balle mata,gashi a lokacin cikinta ko wata tara bai gama shiga ba, Dama kuma matan gidan ba shiga shiyan juna suke yi ba balle Allah ya kawo mata wani,dama ace Goggo Badejo na nan ne,to sai dai shekaran jiya ta koma, Tana cikin haka ne Allah ya dawo da Jauro sai dai lokacin ko magana bata iya yi,gashi jini duk ya bata wuri, Duk da kasan cewar shi yaro a lokacin yasan jini,domin yasan lokacin da Mamar su Moha suka sai Binta asibiti lokacin da take zubar da jini, Dan haka da sauri ya fita yayi gidan su Moha,sai dai cikin rashin sa'a bai tarad da kowa ba a gidan,domin kuwa sun je suna a wani ruga dake gaban nasu, Hakan ne yasa da gudu ya dawo gida ya shiga shiyan Binta,wacce ke zaune tana cin abinci,tsabar rudewa har yana mata ƙwallo da kofin ruwa dake gabanta, Aikuwa ba tayi kasa a guiwa ba wurin dauke shi da mari"kai wani irin ɗan b.... Yaro ne,baka ganin gabanka ne"ta tureshi tana daga kofin ruwan gabanta"maza tashi ka barmin shiyana,kafin in balla ka,hala ma leken Asiri uwarka ta turo ka min" Kuka ya fashe da shi domin marin ba karamin shigar shi yayi ba, Duk da haka sai da ya ɗan maso kusa da ita cikin kuka yace"Innan Ɗan Fodiyo dan Allah kije ki duba Inna ta ba tada lafiya jini ya bata ɗakin mu " "Me kace? Nan ya kara maimaita mata abinda yace, Wani harara ta zuba mai,wanda yasa sai da ya matsa baya" Dallah matsa ka ban wuri,ni lokacin da ciki na ya zube ina ce mamarka tana nan kuma tana kallo,dan haka ita ma nata cikin ya zube,taji yanda naji, fitar min a shiya munafiki"ta faɗa tana nuna mashi kofar fita, Da kuka ya fita ya koma shiyan su,zuwa yayi ya tsaya a kanta yana kallon yanda take fitar da numfashi da kyar, Tsugunnawa yayi a gabanta yana kuka ya rike hannun ta"Inna,Inna"ya kira sunan ta, Da kyar ta iya buɗe ido ta kalle shi, "Na je kiran innar su Moha babu kowa a gidan,da zasu kaiki inda suka kai Innan Ɗan Fodiyo, Itama na naje kiranta tace ba zata zo ba," Gani yayi ta maida ido ta kara lumshewa,jijjigata ya yi"Inna ki tashi muje inda aka kai Innan Ɗan Fodiyo ke ma zaki samu sauki"ganin bata buɗe ido bane yace"bari na je na faɗawa Innan su Yabbale, Sake hannunta yayi ya fita da gudu,bai tsaya ko ina ba sai shiyan Kande..... *🍂JAURO🍂* (MAI ANGUWA) Story & Writing By JIDDARH UMAR 🌟🌙🌙🌙🌙🌙🌙🌟 *🌙✨MOONLIGHT WRITER'S ASSOCIATION🌙✨* https://m.facebook.com/Moonlight-writers-association-109698351308376/ *'''We are the moonlight writers we shine all over the world.''🌍'* ✍️✍️ بِسم الله الرحمن الرحيم ~~~~~~~💞💞~~~~~~~ *Ban yarda wani ko wata su saka min littafi a shafin su ko su mai da min littafi Audio ba tare da izini na ba* *10* Bai tsaya ko'ina ba sai shiyan kande, A lokacin tana kicin tana tankaden gari,da sauri ya rike hannun ta"Innan Yabale ɗan Allah ki zo ki duba Inna ta bata magana kuma jini ya bata ɗakin mu," "A'a Jauro sake ni kar kasa na zubar da garin tuwo," Matsawa gefe yayi ya tsaya yana kallon ta har ta kammala tankaden ta sannan ta kalleshi,ganin har yanzun kuka yake,"me ya sameta " "Ni ma ban sani ba,sai dai bata magana" Tsaki taja tana kallon aikin dake gabanta,gashi har ƙarfe biyu ta wuce ko tuwo bata gama ba, Kara kallon shi tayi"Jauro,ina ganin ka je kawai idan na gama girki zan zo na same ka" Gyada mata kai yayi yana juyawa cike da fatan ta gama da wuri ta zo, Har ya kusa fita daga shiyan ta kuma kiran sunan shi, Dawowa yayi, "Jinin da yawa yaje zuba ne? Ta tambaya, " Eh da yawa ne" "To karka damu yanzun zan zo kaga har nayi talge saura tukawa sai nayi miya, Nan ma kai ya gyada mata, " Yauwa to ka faɗa ma Inna Mari kuwa? Girgiza kai yayi, "To kaje itama ka faɗa mata ko akwai wani iccen da zata ba ka sai ka jika ma innar ka,yi maza ka tafi" Da sauri kuwa ya fita, duk da yana tsoron shiga shiyan sai da ya leka dan ya gani ko Binta bata tsaka gida,sai dai tana ma zaune ne a tsakar gidan, Rasa yanda zai yi yayi dan haka dole ya samu wuri ya tsaya a ƙofar gidan yana jiran ya gani ko Allah zai sa ta shiga cikin daki, A haka sai da ya kwashe kusan minti talatin kafin ya samu ta shiga daki, Da gudu kuwa ya shige cikin gidan yana shiga dakin Inna Mari,wacce ke zaune tana saka mafecin rufe ƙwarya, Allah sarki yaci kuka har hawaye ya bushe a idon shi,muryanshi ya shake baya fita sosai, Tsugunnawa yayi a gabanta yana rike hannun ta"Inna Mari ɗan Allah ki taimaki Inna ta bata magana,sannan akwai jini a dakin mu,ɗan Allah muje ki ganta" Ture shi tayi"kai matsa ka ban wuri,ni bani iya zuwa ko'ina dan yau da ciyon kafa na tashi ba zan iya zuwa ko'ina ba dauko min wancan ledan " Da sauri ya dauko mata ledan, Wani kullin magani ta ciro ta mika mai"amsa jeka jika mata ka bata tasha,ƙila nakuda take yi" Amsa yayi yana kallon ta"to ba zaki je ki dubata ba Inna " "Kai me yasa ka cika kunata je ka kai mata kawai ai tasan yanda zatayi dashi" Tashi yayi ya fita daga dakin,yana kallon mugun kallon da Binta ke bin shi dashi,sai dai tunda ya kalle ta sau daya bai kara yarda ya kalle inda take ba har yabar shiyan, Yana shiga shiyan su da sauri ya karasa inda take kwance yana kiran sunan ta,sai dai wannan karon ko motsin da take yi da ido bai ga tayi ba, Girgizata ya shiga yi"inna,Inna,ki tashi ga magani na amso maki,gashi ki tashi ki jika,Inna Mari tace kinsan yanda ake amfani dashi,"tashi yayi ya fita tsakar gidan su inda take ajiye kwarya,daya ya dauka ya dawo inda take kwance "Inna ga kwarya na dauko tashi ki jika maganin kisha" Nan ma shiru babu amsa, Kallon ta ya tsaya yana yi kamar mai tunani,ya dauki lokaci mai tsayi yana kallon ta,kafin a zuciyar shi ya raya mashi ƙila bacce take yi bari ya jira har ta tashi,sai ya bata maganin,nan ya ƙara ɗaukar ƙwaryan ya rungume yana kallon ta, A wannan lokacin ne kuma wani barci mara daɗi ya ɗauke shi mai tattare da yunwa. Ana cikin haka ne Baffa Dottiya ya dawo misalin karfe biyar na yamma, Tunda ya doso cikin gidan gaban shi ke faduwa,sai dai bai kawo komai a rai ba,domin duk kwanan nan abun da yake yawan ji kenan, Yana ɗaga labulen dakin wani irin karnin jini ne ya daki hancin shi wanda yasa da sauri ya saki labulen ba tare daya shiga ba,dan shi mutum ne mai kyankyami baya shiri da ƙarni, Halima kuma macce ce mai tsafta sosai ga son kamshi,ko yaya ne ba ka rabata da irin turaren nan na mutanin da wanda suke amfani dashi, Mamaki ne ya kama shi,dan haka sai bai shigaba ya tsaya a wurin yana kiran sunan ta,wanda hakan ne ya tayar da Jauro, Missike ido yayi yana kallon ta,har yanzun dai barcin take yi,dan haka zuwa ya ƙara yi inda take yana jijjigata tare da kiran sunan ta,"Inna ki tashi Baffa ya dawo,gashi can yana kiran ki"ganin wannan lokacin ma bata motsa bane yasa kawai ya tashi ya fito, Kallon shi Baffa yayi "Innar ka fa? " Baffa tana daki,tun Dazu nake tada ita kuma taki tashi,yunwa nake ji" Ji yayi gaban shi ya yanke ya ƙara faɗuwa, Bai ce mashi komai ba ya kutsa kai cikin ɗakin,sai dai a irin halin da ya iske matar tashi a ciki ne yasa saura kaɗan jiri ya yarda shi, Har ji yake numfashin shi na ƙoƙarin daukewa,gaɓoɓin jikin shi shi sun sake, A hankali kamar wanda ke tsoron karasawa wurin da take ya isa, Hannun ta ya ɗaga,sai dai yana sakewa hannun ya faɗi ragaf, Duk inda yake tunanin zai ji numfashi a jikinta ya taɓa sai dai dip babu alamunsa,wanda dama tun ganin farko daya daura ido a kanta ya tabbatar da cewa yayi rashi babba, Kallon ɗan nashi yayi,"je ka kira mutanen gidan nan" Harya juya da sauri ganin Baffa shi na hawaye,sai kuma ya dawo yana kiran sunan shi"Baffa dazu naje na faɗi ma Innar Ɗan Fodiyo tazo Inna ta ba tada lafiya kuma a kwai jini a dakin mu shine taki zuwa kuma harda Marina tayi,na san yanzun ma idan na je dukana zata yi,ita kuma Innar Yabale tace idan ta gama abinci zata zo" Ji yayi wani irin hawaye masu raɗaɗi sun sauko mai,menene amfanin irin wannan rayuwar,me amfaninta,ace maka mutum na zubar da jini tun ƙarfe daya na rana,yaro yaje ya faɗa maku amma ba wacce ta iya cewa bari in Leko in duba kai koda Akuyar ka akace tana zubar da jini ka je ka gani balle a ce mutum,haba,haba,wannan rashin imani ya ɓaci, "Ka fada ma Inna Mari kuwa" "Na faɗa mata tace ba zata iya zuwa ba saboda ƙafarta na ciyo,sai dai ta bani magani na kawo ma inna ta jika,sai dai ina ta tada ita amma bata tashi ba" Bai san da idon fassaran da zai kalle ahalinsa ba,bai san da wani kalan suna suka dace ya kira suba,sai dai abu ɗaya,shi ne yana masu fatan tarwatsewa tankar yanda suka tarwatsa rayuwar shi,suka ki kula matar shi da danshi alokacin da suke nimam taimako, Shi kuma insha Allah sai ya basu mamaki,ba zai nima taimakon su ba koda da menene, Tashi yayi ya dauki fura ya dibo kindirmu a inda suke ajiyewa ya dama na ɗan na shi, Yana gamawa ya haɗa wuta ya saka ruwan dumi,sannan ya watsa magarya aciki tamkar yanda wani malami ya nuna masu a lokacin da mahaifin su ya rasu,kuma ya masu bayani yanda zasu mace,dan alokacin shine ma ya tambaya in macece ya ake mata, Sai da ya gusar da duk wani najasa dake dakin dakuma wanda ke jikin ta,sannan ya mata wanka tas, Ya ce ma Jauro "zauna kusa da Innar ka bari in je in dawo" Kallon Baffan na shi yayi "Baffa yaushe zata tashi" Guya kai yayi ya share hawayrn shi"karka tada ita kaga ba tada lafiya bari naje na dawo, Yana fita gidan limamin dake basu sallah yaje,dama ba'a rasa likafani a wurin shi,dan haka faɗa mashi yayi,abinda ke faruwa dashi har izuwa mutuwar Matar shi ya karasa faɗa yana fashewa da kuka, "kamar yanda suka ki kula ɗana alokacin daya je niman taimakon su,ina fata kar Allah ya taimaka masu a ko wacce hanya,ya bar su da iyawarsa,ya tarwatsa su" Da sauri malamin ya rufe mai baki"haba Dottiya me yasa kake irin wannan addu'ar ga ahalin ka,kaga irin haka bai da kyau,ko ba komai ƴan uwan ka ne hakan be kama ta ba" "Malam yanzun damuwa ta daya,shine Jauro,wani irin rayuwa ɗana zai yi,bana son dana ya tashi da irin wannan hali nasu,bana so yayi koyi da dabi'un su,da nasaka raina akan mahaifiyarsa ce,kuma sai gashi ta riga tafiya ta barni" "Me kake faɗa haka ne Dottiya,insha Allah kana tare da ɗan ka,kai zaka reni abin ka, " Girgiza kai yayi,yana ƙara zubar da wani hawayen wanda yake jin zafin shi har cikin zuciyar shi,"naso haka,naso ace hakan zai kasan ce,sai dai kuma...... " Sai yayi shiru ya kasa karasa fada,rike hannun malamin yayi"ɗan Allah ina rukon wata Alfarma a wurin ka" Cikin tausayawa yace "ina jinka Dottiya" "Malam dan Allah ina rokan ka dauki Jauro acikin ɗaliban da kake koyarwa,ka tsaya mashi yayi ilimin addini,karya zamo kamar mu dan Allah Malam" Jinjina kai yayi"na maka Alkawari Dottiya,insha Allah zan tsaya masa ya samu ilimi addini yanda ya kamata,ka kwantar da hankalin ka,kaga mutane har sun taru domin na aika daya daga cikin yarana suje suyi shela za'a sallar gawa a gidan ku,taso muje a samu a kai ta ɗakinta na gaskiya kafin magriba tayi"...... *🍂JAURO🍂* (MAI ANGUWA) Story & Writing By JIDDARH UMAR 🌟🌙🌙🌙🌙🌙🌙🌟 *🌙✨MOONLIGHT WRITER'S ASSOCIATION🌙✨* https://m.facebook.com/Moonlight-writers-association-109698351308376/ *'''We are the moonlight writers we shine all over the world.''🌍'* ✍️✍️ بِسم الله الرحمن الرحيم ~~~~~~~💞💞~~~~~~~ *Ban yarda wani ko wata su saka min littafi a shafin su ko su mai da min littafi Audio ba tare da izini na ba* *11* Duk wannan abunda ake yi matan gidan ba su sani ba,har Matan liman su biyu suka zo suka taimaka mai aka saka mata sutura, Shine fa Ɗan Fodiyo yaje cikin gidan su yake fadama Binta yaga Baffa Dottiya na kuka, Sai ga Kande ta shigo da gudu tana ihun kira Inna, "Waiyo jama'a mun shiga uku Halima ta mutu,Inna,Inna" Da sauri ta fito ɗaki har zanin jikinta na faduwa "ke wata Halima ce ta mutu? Kuka ta fashe dashi tana zama abakin dakalin wurin tare da daura hannu a kai" Innar Jauro,waiyo Allah kaicona dazu yaron nan ke bina akan na zo na duba Uwar shi tana Zubar da jini,amma ban kula shi ba nace ya bari sai na gama girki,ashe dai mutuwa zata yi "ta karasa faɗa tana fashewa da wani sabon kukan" Gashi can yanzun za'a fitar da ita,saboda bakin hali irin namu ko sanar damu abinda ke faruwa Dottiya bai yi ba,sai makota ya gaiyato suka taimaka mashi" Inna Mari da sauri ta doshi hanyar waje har tana tuntuɓe, Koda ta shiga shiyan Halima har an fito da gawar, Kuka ta saka tana rike makaran"yanzun shikenan Halima tafiya zaki yi ki barmu,Allah sarki mutuniyar Arziki dana sani dazu ai koda rarrafe ne dana gangaro,ashe bamuda rabon ƙara ganin juna ne" Dottiya ne ya kalle wadanda suka taya shi daukar makaran"kai mu tafi dare na yi " Ai kuwa cire hannun ta daya yayi daga jikin makaran sukayi gaba da ita, zama tayi a wurin ta dafe kai domin ba karamin sanyi jikinta yayi ba yau,har balle irin kallon da taga Dottiya na mata,tabbas tasan bata kyauta mai ba a matsayin ta na uwa,bai dace ta tsaya a bangare daya ba,bai dace a lokacin da yaro yazo mata da maganar mamar shi na zubar da jini taki sauraren shiba,yanzun wani irin kallo mutane zasu mata,ita kan da tasan mutuwa Halima za tayi wallahi da taje ta ganta. A waje kuwa cikin aminci aka yiwa Halima sallah sannan aka kaita gidan ta na gaskiya, Allah sarki Dottiya sai da aka daga shi daga jikin kabarin ta, Kwana uku akayi zaman makoki wanda duk lokacin yana manne da ɗan shi,duk zaman da akayi ba laifi yana tare dasu Bube suna karɓar tare,sai dai matan duk wacce ta mai gaisuwa idan ya amsa so daya baya kuma amsawa har ta da Inna, Sai dai abin mamaki duk wannan abinda ya faru Binta ko sau daya bata taɓa lekawa da sunan gaisuwar rasuwar Halima ba,har ta su Badejo dake aure wani gari sun zo gaisuwa amma ita ko kofar shiyan Halima bata leka ba har yanzun da nake magana. Bayan sadakan uku ne shanayen Baffa Dottiya suka iso da daddare, Fita yayi ya same su,dan lokaci kusan ƙarfe ɗaya da rabi ne na dare, Zama yayi kusa dasu yana masu bangayi, ɗayan ne mai suna Manu yake tambayar shi "ina uwar ɗaki na"dan sunan da yake kiran Halima dashi kenan,yana dariya yace" Yanzun nasan ta kusa haihuwa,Jauro ya samu kani ko ƙanwa" Daya daga cikin su ne yace"to na dai rigaka Manu in dai mace ce ni za'a ba auren ta" Su biyun dariya suka yi,dama kuma su huɗu ne masu masa kiyo to biyu sun kwanta dan lokacin biyu tayi, Ganin ya dukar da kai yayi shiru ne Manu ya ce"Uban daki na ni kam ba kada lafiya ne naga wallahi duk kayi wani irin rama kayi baki," Dago kai yayi ya kalle su yana sauke ajiyar zuciya, ,"Halima ta riga mu gidan gaskiya,Allah ya karɓi abinshi " Ji kake wurin yayi wani tsit na ɗan lokaci tamkar babu mutane a wurin kafin Manu yace"ni fa Innar Jauro nake magana" Dafa kafadarshi yayi "kwarai kuwa ita,ni kaina na kasa yarda gani nake kamar a ko wani lokaci tana iya dawowa bayan da hannuna na saka ta acikin kabari" Yakubu ya fashe da kuka yana salati,domin su biyun sun kasance yan dakin ta sosai na tsayin shekaru huɗu da sukayi yawo, Sosai yaran suke jajanta rashin Uwar dakin nasu, "Ina roƙon wani alfarma mai girma a wurinku" Duk mai da hankali kanshi suka yi, "muna jinka uban ɗakin mu" A jiyar zuciya mai ƙarfi ya kara sauke,yana jin wani irin ciyo da raɗaɗi mai kuna yana taso mashi daga ƙasan zuciyar shi, "Alfarman da nake nima babba ne wanda bansan ko zaku iya rikewa ba ko ba zaku iya riƙewa ba,abu ɗaya na sani shine na yarda daku har cikin zuciya ta,ba ni da wanda zanba amana sama daku,idan har kunci amana ta Ubangiji na kallo domin ni saboda yarda na bayar,idan kuma Allah ya baku ikon rikewa Alhamdulillah, Ina so ku dauki Shanu garke ɗaya,raguna da tumakai rabin garke,ku tafi da su " Duk kallon mamaki suke mai,"mu tafi dasu ina,bayan gashi mun dawo gida,yanzun lokacin damuna ne ai ba rani ba" "Haka ne,sai dai kuma ina da dalilina na yin haka,Manu ba ni da lafiya sosai,ako wani lokaci komai na iya faruwa dani,ƙila ana iya kwantawa dani ba'a tashi da ni ba, Abinda nake matukar tsoro kenan, Saboda ƴan uwana,nasan da zaran bana raye zasu karbe komai na dukiya ta daga hannun ku,nasan ba zasu ajiyema ɗana komai ba,kuma koda ya girma ba bashi zasu yi, Shi yasa nake son ku tafi dasu,ku yi nisa dasu,in so samu ne kuna iya komawa dasu nahiyar ku ta Niger daga nan har zuwa sanda Jauro zai mallaki hankalin shi," Yakubu ne yace "uban gidana kamar nan da shekara nawa kenan? " Yanzun shekaran Jauro shida,yana ƙoƙarin shiga na bakwai,dan haka nan da shekara Goma sha biyar" Duk kallon mamaki suke mai,dan basu zata zai ja da nisa ba, "Amma kana ganin bai yi yawa ba" "A'a bai yi yawa ba,sannan bana son ƴan uwa na su sani,kawai in so samu ne ku yi yanda nace sannan ina son ku tafi tun kafin gari ya fara haske dan bana son su san iya adadi abinda kuka tafi dasu" Allah sarki,a haka suka karɓi wannan amanar da Yakubu da kuma Manu,sannan cikin wannan daren suka bar rugar da taimakon shi Dottiya,suna mashi fatan samun tsawon rai don coyon hanta mai tsanani yake fama dashi wanda yayi chronic sosai. Washegari da safe da kanshi ya shirya Jauro kuma ya raka shi har gidan su Moha inda zasu tafi Boko da keken shi, Bayan ya dawo ne ya tafi shiyan Bube wurin Inna domin sanar da ita isowar shanayen shi. *🍂JAURO🍂* (MAI ANGUWA) Story & Writing By JIDDARH UMAR 🌟🌙🌙🌙🌙🌙🌙🌟 *🌙✨MOONLIGHT WRITER'S ASSOCIATION🌙✨* https://m.facebook.com/Moonlight-writers-association-109698351308376/ *'''We are the moonlight writers we shine all over the world.''🌍'* ✍️✍️ بِسم الله الرحمن الرحيم ~~~~~~~💞💞~~~~~~~ *Ban yarda wani ko wata su saka min littafi a shafin su ko su mai da min littafi Audio ba tare da izini na ba* *12* Sallamarh yayi yana shiga cikin ɗakin nata, Amsawa suka yi suna matsa mashi dan ya samu wurin zama, Saida ya fara gaida Inna Mari kamin ya juya ya gaida su a jam'i,sannan ya zauna, "Nikam Dattiya me ke damun ka ne,naga duk ka lalace"cewar Baffa Sanda. " Babu komai," "Amma ka yi kaman wanda ke cikin rashin lafiya" Wannan karon Bube ya tambaya, "Ya dai kamata ka cire Halima arai haka nan,tunda kasan dai wanda ya mutu ba shi dawowa,dubi yanda ka kanjame,ai da irin wannan tunanin da zai iya hallakaka gara kawai kayi aure ko zaka rage tunani" Shiru yayi yana kallon Inna,ko fa sati ɗaya matarshi bata gama cikawa da rasuwa ba,amma shine har take dauko mai batun wani aure,ya tabbata idan da yarta ce ta mutu ai ba zata ce ma mijin yar yaje yayi wani aure ba, "Inna shanaye na sun iso da daddare" Washe baki ta hau yi"kai abu yayi kyau,anjima kuwa zan saka yara su kaini naje na gani" Kallon ta yayi yana mamaki hali irin na Uwar su,"ke da kafarki ke ciyo,ko ina baki iya zuwa shine har zaki iya zuwa ganin dabbobi,ko da yake dabbobi ne ai sunfi mutum daraja " Duk shiru suka yi,domin sun fahimce inda zancen nashi ya dosa, "Yanzun Dabbobin ka sunkai nawa Dottiya,nasan sunyi Albarka? Baffa sanda ya tambaya dan kawai ya dauke shirun da ɗakin yayi, " Garke daya ne da guda dari biyu,sai tumakai gudan saba'in" Duk kallon mamaki Inna da Bube suke mai"amma nan kace min shanayen ka sun wuce garke biyu, bancin tumakai"Cewar Bube kamar a hasale, "Na dai faɗa ne kawai amma iya abinda nake dasu kenen,ko dai basu yi Albarka bane?ya faɗa fana kallon su shima,dan bai gama fahimtar in da suka dosa ba da wannan tambayar da kuma zafin rai na Bube, Sanda ne yace" A'a abu yayi Albarka,kai da ka wuce garke daya,babu laifi ai,Allah ya saka masu Albarka,idan munbar nan zamu je mu duba su" Bai basu amsa ba sai ma tashi da yayi ya bar su a dakin. A haka dai yaci gaba da lalla rayuwar shi yayin da duk safiya idan an idar da sallah zai kai Jauro wurin Malam liman ya ɗauki karatu zuwa ƙarfe bakwai na safe kafin ya dawo ya tafi Boko,nan ma in ya dawo zuwa ƙarfe hudu yake sake tura shi islamiyan yamma, Ana cikin haka ne suka wayi gari da tsananin tashin hankali a wannan gidan,wanda shine yayi sanadiyar sauya rayuwar Jauro,ya mai dashi daga sama ya dawo kasa sannan a ƙasan ma ya kife,wato rasuwar Mahaifinshi Dottiya,wanda suka kwanta dashi sai dai basu tashi dashi ba, Mutuwar ta shiga mutanen gidan sosai har balle tsohuwa Inna Mari,wacce rabon da amata rasuwa tayi kuka irin haka tun mutuwar mijinta, Sunyi Jimami na tsayin kwana uku kafin su wassake, Allah sarki Jauro,duk da yana yaro yanda yayi kuka a mutuwar mahaifinsa bai yi a lokacin daya rasa mahaifiyar sa ba,domin kuwa a lokacin mahaifinsa ne ke dauke masa kewar Innar sa,baya bari yayi kuka rashinta, Yanzun kuwa yana wurin ƴan uwan mamarshi ne da suka zo gaisuwa, Randa aka gama sadakan uku kuma da zasu koma suka roƙi Inna Mari Alfarma ko zata basu dama suna son su tafi da Jauro ya zauna a wurin su, Har fa matar nan ta amince,sai ga Baffa Bube ya shigo a jigace har yana kumfar baki,kan cewa me yasa za'a basu Jauro su wuce dashi,ai suma suna da halin da zasu iya riƙe shi,kuma shi zasu dinga gani suna tuna ɗan uwansu,dan haka su tafi kawai shi zai rike Jauro a hannun shi, Babu kalan rokon da basu mashi ba amma ya rufe ido yaƙi,karshe ma sai bin bayan shi Inna Mari tayi, Wannan abun yaba ƴan Uwan mahaifiyar sa haushi,akan irin maganganun da Bube ya masu,wanda yaja suka yi fishi tare da Alkawarin basu kara tako ƙafar su inda suke,sai dai in Allah ya raya Jauro da kanshi zai zo ya nime su ta yanda basu isa su hana shi zuwa ba, Da wannan bacin ran suka wuce,domin dama su burinsu su dauki ɗan ƴar uwarsu su riƙe saboda sun san irin zaman da ake yi a wannan gidan, To sai gashi abin bai yuba,sai dai kawai su bishi da Addu'ar Allah ya raya shi,ya bashi haƙuri da juriyan zama a cikin waɗannan mutanen,wannan kenan. Bayan wucewar su ne Inna ta kalle shi "to yanzun kai Bube ka nada in da zaka ajiye yaronnan daka hana a tafi dashi,ka dai san halin matar ka da bakin hali," "To Inna ba sai ya dinga kwana a dakin su Ɗan Fodiyo ba,ai yaron da wayonshi tunda ba kashi zata dinga wanke mai ba,abinci kuma wanda kowa yaci haka zai ci,to me aciki,kenan baki gane me mutanin nan suke nufi ba,so suke yanzun da sun karbe shi zasu ta da fitinar a raba gado a basu nashi su tafi dashi gaba ɗaya,shi yasa na hana" Kallon shi tsohuwar keyi"to nikan in haka ne me zai hana a kira Malam liman a gobe yazo ya raba gadon nan kowa ya huta," Turbune fuska yayi "A'a ba sai an ƙirashi ba,ki bari ni zan kira malami na zai zo ya raba da kanshi,ko a cikin gari ba karamin babban malami bane" "To shikenan hakan ma zai fi,yanzun dai sai ka faɗa ma ɗan'uwan ka,saboda yasan abinda ake ciki" Haka kuwa aka yi,a ranar su da basu magana da juna sai gashi saboda abin duniya suka shirya, Washegari da kansu suka je suka dauko wannan malamin a cikin gari, A dakin Inna aka zauna za'ayi rabon,bayan sun je sun kirga dabbobin,wanda suke garke daya da guda Dari biyu, Sai tumakai guda saba'in, Kaso na farko da aka fara yi,shine Baffa Bube aka bashi shanaye guda dari huɗu,shima Sanda aka bashi Dari huɗu,ya rage dari huɗu,shi ma aka bama Jauro dari biyu,Inna Mari guda Dari,sauran ɗari,aka ba Goggo Badejo guda talatin,sai Goggo Halira ita ma guda talatin,ya rage guda Arba'in,Malam mai rabon gado ya ɗauki guda goma sha-biyar,ya rage ishirin da biyar,aka ba Inna Kande guda Goma,Inna Binta ma goma,ya rage biyar,aka ba Yabale guda ɗaya,Dotti ɗaya,yaran Baffa Sanda kenan,sai Ɗan Fodiyo daya,Bakari daya,yaran Baffa Bube, Ɗayan daya rage kuwa za'a sai da a raba kudin kowa a bashi, Tumakaima irin rabon da aka masu kenan wanda a ƙarshe Jauro ya tashi da guda goma. Baffa Bube ne yace shi zai rike gadon Jauro har ya girma,shi kuma Baffa sanda yace sam bai yarda ba sai dai a raba kowa ya rike ɗari ɗari,in yaso in ya girma sai a bashi,in kuma bai yarda ba ya tattaro mai da Jauro da dukiyar shi duka shi zai iya rike su, Ganin fitina na kokarin kara tashi ne yasa Inna Mari tace su raba kowa ya ɗauki dari su rike mai kafin ya girma, Sannan idan yayi sati a shiyan Binta yayi Sati a shiyan Kande,yan da aka tsayar da magana kenan,sannan yau zai fara ne da shiyan Binta,tunda dama jiya a dakin Inna Mari ya kwana tare da goggonnin shi,to suma yau zasu wuce.... *🍂JAURO🍂* (MAI ANGUWA) Story & Writing By JIDDARH UMAR 🌟🌙🌙🌙🌙🌙🌙🌟 *🌙✨MOONLIGHT WRITER'S ASSOCIATION🌙✨* https://m.facebook.com/Moonlight-writers-association-109698351308376/ *'''We are the moonlight writers we shine all over the world.''🌍'* ✍️✍️ بِسم الله الرحمن الرحيم ~~~~~~~💞💞~~~~~~~ *Ban yarda wani ko wata su saka min littafi a shafin su ko su mai da min littafi Audio ba tare da izini na ba* *13* Kamar yanda suka tsara mashi haka suka barshi a shiyan Binta inda zai yi Sati ɗaya, Bayan wucewar Goggonnin shi ne ya koma dakin Inna Mari ya zauna,dan yaje shiyan su babu kowa kuma shiyan ma a kulle yake, Da lokacin cin abincin rana yayi kuwa haɗa masu aka yi a babban kwanu shida su Dan Fodiyo,sai dai fa kafin yayi loma ɗaya sunyi uku,dan Innar su tace karasu bari ya cinye ya bar su,su dinga yin ƙaton loma,idan ya kusa karewa su buɗe hannu su kwashe duka, To abinda ya faru kenan a lokacin da suke cin abinci,yanda kasan da Awaki yake cin abinci haka suka mai,domin kamar basu haɗiye na bakinsu suke saka wani,gashi dama abincin bai da yawa,koda ya duba kwano tuwo ya kafe tas,amma kwata_kwata loma huɗu ya yi, Tsayawa yayi yana kallon su ya kalli kwanun,ga kuma katon tuwo a hannun su suna gutsura suna ci,suna mashi dariya, Hannun ya mika "ɗan Allah ɗan Fodiyo danmin tuwonka ka ga ni ban ƙoshin ba" "Ai ni ma ban ƙoshin ba,ka dauki kwanu ka kai inna ta kara mana" Baicimusu ba kuwa ya dauki kwanu ya shiga daki inda Binta ke zaune,ɗan rabewa yayi dan Allah ya gani yana matukar tsoron wannan matar,domin ko kaɗan bata mai ragi, "Inna Binta ban koshi ba a ƙara min abinci" Wani irin mugun kallo ta bishi dashi"tunda ubanka dake kabari ya kawo uwarka dake kabari ta zo ta dafa ba,ai dole kace baka koshi ba,to na waye kake son a baka," Kafin ma ta ƙara ɗaura mai wani zagi yayi waje da sauri ya ajiye kwanun wurin wanke-wanke,dakin Inna Mari ya shiga,a lokacin ita ma tana cin nata abincin,haka ya zauna a gefe yana kallon ta,sai da tace kusan rabi sannan tace zo ka ɗauka,ai kuwa jikin shi har rawa yake da farin ciki ya ɗauka "na gode inna" Kallon shi tayi"ka gode me,je ka ajiye min abinci a can domin anjima shi zan ci " Dan bata fuska yaro yayi "inna ba cewa kika yi na ɗauka na ci ba? " Ni ko me zai sa na dauki abincina na baka bayan kaci tare da yan'uwan ka" "Inna ban koshi ba,yunwa nake ji" "To ai ka ga matsalar kenen,shi yasa babu kyau ka sangarta ɗa da ci,saboda halin rayuwa,iyayenka suna ganin kai kaɗai ne a gaban su sun buɗe makarantar ciki da cin abinci yanzun gashi yanda lamari ya kasance,wa zai iya ci da kai,ni dai ba zan iya ɗaukar abinci na ina baka baka ba,dan ma kar ka saka rai a kan haka,a jiyemin kwanun tuwo na a can anjima shi zan ci nima dan ba gama abinci dare da wuri za'a yi ba,in ma taga dama tace ba tayin na daren,gara na ɓoye nawa duk yanda yama to" Bai ce mata komai ba ya ɗauki tuwon ya ajiye mata a gefe sannan ya fito, Yana fito ya haɗu da Binta a tsakar gida, Kallon ci tayi cikin harara wanda ta ya riga ya sani bata taba mai kallon arziki sai dai na harara ko yaushi "kai yan zun Jauro dan baka da kunya ni kake jira ka ci abinci na wanke maka kwanu,to baka isa ba,maza zo ka yi wanke-wanke kafin na canza maka kamanni,idan ka gama ka share tsakar gida,dan ni ba zan iya aiki kana zaune ina kallon ka ba kamar wani mara amfani" Ba yanda ya iya cikin rawar jiki ya shiga tattara duk kayan da aka ci abinci har na kofar ɗakinta wanda anan ne yaga su Ɗan Fodiyo zaune a cikin dakin da ƙaton malmalan tuwo a gaba suna ci, Bai ce komai ba dan ya fahimci ko ya roka ba samu zai ba, Tunda yake bai taɓa yin wanke-wanke ba amma yana ganin yanda Innar shi ke yi,dan haka shima zama yayi ya fara wankewa a hankali,duk da haka wanke-wanken babba da yaro ba ɗaya ba,balle wanda bai taɓa ba ba,dan haka wasu sun wanku wasu basu wanku ba,a haka ya gama wanke-wanke,sannan ya fara shara wanda shima bai sharu da kyau ba, Ai kuwa a kan wannan wanke-wanke da shara sai da ta zane shi sosai wai dan mugunta ne yasa yaki mata aiki da kyau,sannan tasa ya ƙara dibo ruwa tana tsaye akan shi tasa ya ƙara wanke wa,idan bai fita ba ta sakar mashi rankwashi,da haka ya gama da kuka da hawaye da majina,shara kuwa yana yi tana biye dashi da bulala a hannu,duk inda ya bar datti sai ta zauga mai tace ya koma ya share,da haka dai ya gama sharan,sannan ya lallaba ya bar cikin gidan,dan gani yake kamar kamar yana fita ya rabu da wannan bala'in na binta kenan sannan yana zuwa shiyan su zai tarar da Innar shi da kuma Baffan shi suna jiran shi, Hakan ne yasa ya koma kofar shiyan su da aka kulle ya zauna,dan yata tura kofar taki buɗewa,zama yayi ya fara kuka yana kiran sunan Mamar shi,dan bai san inda ta je ba, Yana cikin haka ne har barci ya dauke shi,wanda bai jima ba yaji ana ta da shi, Bude ido yayi ya kalli me tada shi,daya ne daga cikin yaran Malam Liman, "Jauro Malam yace kazo lokacin sallah yayi sannan za'a shiga Islamiya idan an fito sallah" Tashi yayi ya bi ya ban yaron suka je har gidan Liman,a zauren yaron ya ajiye shi ya wuce dan shirin dauro Alwallah, Yana shiga ya gai da Malam sannan ya zauna a gefe, Kallon yaron yayi cikin tausayawa domin maraici ba karya bane,dubi cikin kwanaki kalilan yanda ya zube ya lalace,yasan ladan dake tattare wurin renon maraye da kuma azaban dake tattare akan wanda ya azabtar dasu ko kuma wulakansu,koda kuwa kuka mutum ya saka su, Kwanun abinci dake gefen shi ya jawo ya mika mashi, "Ɗauka kaci,idan ka gama ka zo ka same ni a masallaci" Daukan kwanun yayi ya buɗe,lafiyayyen sakwara ce da miyar ganye, Ai kuwa nan ya fara ci,hannu baka hannu kwarya, Sai da yaji babu wurin zubawa sannan ya hakura ya ajiye sauran ya sha ruwa, Yana fitowa ya dauki buta yayi alwalah ya shiga masallaci,in da har an tada sallah, Suna idarwa kuma aka fara karatun yamma,wanda sai ƙarfe shida suka tashi, Har ya fito zai koma gida,sai kuma ya koma in da Malam ke zaune yana ƙoƙarin tashi,zama yayi kusa dashi, "Malam"ya kira sunan shi, Shima amsawa yayi yana kallon shi, " Malam ina Inna na da Baffa na suka je,naga shiyanmu a kulle babu kowa,kuma idan naje ina ta bugawa babu me zuwa ya buɗe min,sannan Inna Mari tace sai dai in dinga kwana a shiyan su ɗan Fodiyo,ni yaushe ne su Inna da Baffa zasu dawo,ina son in gan su,ko kuma ka kai ni in da suke" Jikin shi gaba ɗaya yayi sanyi da kalaman yaron,dole ne ya faɗa mashi gaskiyar menene mutuwa ta yanda zai iya fuskantar gaskiyar duniya da kuma rayuwa,domin yasan ta yanda zai gina rayuwar shi........ *Nagode sosai da Addu'ar ku na ji sauki sosai yanzun kam,sannan masu jiran YAR TSANAR ZINARI zasu samu zuwa anjima insha Allah* *🍂JAURO🍂* (MAI ANGUWA) Story & Writing By JIDDARH UMAR 🌟🌙🌙🌙🌙🌙🌙🌟 *🌙✨MOONLIGHT WRITER'S ASSOCIATION🌙✨* https://m.facebook.com/Moonlight-writers-association-109698351308376/ *'''We are the moonlight writers we shine all over the world.''🌍'* ✍️✍️ بِسم الله الرحمن الرحيم ~~~~~~~💞💞~~~~~~~ *Ban yarda wani ko wata su saka min littafi a shafin su ko su mai da min littafi Audio ba tare da izini na ba* *14* Dafa kafadarshi yayi tare da sakar mashi lallausar murmushi,sannan ya kira sunan shi, "Allah shi ya halicci komai da komai da kake gani a nan duniya,da wanda idon ka ke iya gani da wanda idanun ka ba su iya gani,mutum da Aljani,ice,sama da ƙasa,tsaunuka,rana da wata,zafi da sanyi,iskar da muke shaka,ruwa,abubuwan dake rayuwa a cikin ruwa,Jauro ina nufin komai da komai da kake gani,kuma shine yake amsar su a duk lokacin da yaso,domin ko wani abu da ka gani a duniya kome dadewar shi a duniya yana da nashi iyakar da Allah ya dibar mashi,haka ma mutum yake,duk wanda ka ga ya mutu to ya cika iya wa'adin zaman da Allah ya ɗibar mashi ne a duniya,kuma wanda ya mutu baya taɓa dawowa," "Malam yan zun Inna da Baffa ba zasu dawo ba kenen? " Ba zasu dawo ba Jauro,sai dai abu ɗaya zaka masu wanda zai sa su farin ciki,su san cewa kana son su sosai kana kuma kewar su" "Me zan yi,? " Duk abunda zaka yi kada ka bari sallah ya wuce ka,idan ka yi sallah ka ɗaga hannu ka masu Addu'a,domin Allah mai karɓar Addu'ar bayinsa ne,idan ka masu Addu'ar zai isa gare su,kuma zasu ji daɗi su san cewa lallai Jauro na matukar son su,sai kuma ka dage kayi karatu sosai na Boko dana Islamiya,tunda naga kana da son karatun Boko,gashi kwana biyu ma ka ba je ba,gobe idan Allah ya kai mu ka shirya kabi Moha ka tafi makaranta,ina son in ga ka cika burinka,ka kuma cika burin iyayen ka,kaji Jauro ka dage ka mai da hankali,karka damu da komai da za'a yi ko za'a ce" Jinjina kai yayi duk da a lokacin ya fahimce wasu daga cikin abinda Malam liman ke faɗa wasu kuma bai fahintaba a wannan lokacin amma ya tabbatar yasa kudirinsa akan karatu. Tun daga wannan lokacin ya cire komai a ran shi yasa ma ran shi lallai cewa shi maraya ne wanda bashi da uwa bashi da uba,ba kuma shida dangi,shi kaɗai ke son kanshi,sai dai kamar yanda Malam Liman yace mai Babu maraya sai rago,to lallai ba zai zama raggo ba,zai yi ilimi ta yanda mutane zasu so shi zasu kuma girmama shi,zai zama abinda yake son ya zama da taimakon Allah,wannan shine ƙudirin Yaro mai shekaru bakwai a wannan lokacin, Tun daga sannan ya mai da rayuwar shi tashi shi daya,idan gari ya waye shi zai fito yayi wanke-wanken kwanukan da aka bata ya share tsakar gida duk sanyi duk iska,domin in bai tashi ba ma da bulala Inna Binta ke tada shi,idan kuma lokacin sanyi ne da ruwan randa zata tada shi,shi yasa tunkafin ma ta tashi barci yake kammala mata aikin da zai yi,baya tsayawa ya jira sai an bashi abin karin safe sannan ya tafe makaranta domin yasan ko ya tsaya ba lallai ya samu ba,ko ya samu sai kusan goma na safe,shi yasa ya gwammace ya wuce,in ya dawo ya samu to,in bai samu ba sai tafi gidan su Moha ko Malam Liman a can kam baya rasa abinda zai ci. A hankali rayuwa ke tafiya abubuwa na sauyawa da dama, amma banda gidan su Jauro domin kamar dai yanda yake tun 1999,haka yake babu abinda ya canja a wannan gidan sai ma abinda ya karu, Domin kuwa Inna Binta ta ƙara haihuwa,har ya'ya uku,kamar yanda ita ma Inna Kande ta ƙara har yara biyu,kuma ita ma idan lokacin kwanan Jauro yayi a shiyan ta,to da ita ma ta samu dan aiki,domin ita ba karamar kazama bace,shara wanke-wanke,har ta da wanki shi ke masu,ko da jika jika ne ita be dame ta ba,kuma a haka yake daurewa yake yin duk abinda aka saka shi,domin shi ba yaro bane mai son jiki,to ina ma yaga ta son jiki,wa zai ma son jiki. Batun makaranta kuwa cikin ikon Allah shi ke daukar na ɗaya,domin Jauro irin yaran nan ne da ake kira gifted,in da magana ne akan Mathematic to ba'a magana domin ko malaman su suna mamakin yaron,domin yaron ga shi dai dan ƙauye amma Allah ya bashi, Moha ya riga shi kammala primary har ma ya shiga wata government school anan wanda baida nisa da nan ɗin,yana primary five suka tafi gasa irin wanda ake kai yara,cikin ikon Allah shi yazo na daya,wanda jin daɗin hakan ne yasa wani mutum wanda ya ji an kira da suna Alhaji Abubakar Imam,shi ya ɗauki nauyin makarantar Jauro tun daga Jis one har S.S three kuma a makarantar kuɗi,domin shima ya nada nashi makarantar kuma babba ce ta masu kudi a wannan lokacin, Wannan labarin ba karamin daɗi abin yama Malam Liman ba,Allah sarki har da hawayen shi, Ta ɓangaren Islamiya kuma babu laifi domin har yakai izifi goma sha biyar,. A haka rayuwa ta mike kuma tana tafiya da daɗi da kuma babu daɗi, Shigar Jauro babban makaranta ya saka rayuwar shi sauyawa ta bangarori da dama,ya samu daukaka a cikin ɗalibai da kuma malamai,ba dan komai ba sai dan ilimin shi,sai dai....... *🍂JAURO🍂* (MAI ANGUWA) Story & Writing By JIDDARH UMAR 🌟🌙🌙🌙🌙🌙🌙🌟 *🌙✨MOONLIGHT WRITER'S ASSOCIATION🌙✨* https://m.facebook.com/Moonlight-writers-association-109698351308376/ *'''We are the moonlight writers we shine all over the world.''🌍'* ✍️✍️ بِسم الله الرحمن الرحيم ~~~~~~~💞💞~~~~~~~ *Ban yarda wani ko wata su saka min littafi a shafin su ko su mai da min littafi Audio ba tare da izini na ba* *15* *Bayan shekara goma* A cikin waɗannan shekarun da suka wuce abubuwa da dama sun faru ko ince suna kan faruwa,domin gida ya ƙara cika da yaya,da kuma samari, Ta bangaren halin mutanen gidan kuwa babu abinda ya canja,domin kuwa suna nan a yanda suke,sai ma abin da yaci gaba, Domin kuwa yanzun yan gidan su Baffa Sanda basu isa suyi magana da koda yaro ƙarami bane in dai dan Baffa Bube ne,babu mutunci a tsakanin nin su kamar yanda babu ragi, Baffa Bube dai shikam Allah yayi ya kara Aure,hmmm,sai dai ranar anga hauka tuburan a cikin gidan, Sai dai shi mai gidan yace bata isa ta hana shi abinda yake so ba,kuma Amarya dole ta zauna, Ganin da gaske yake ne yasa ta tattara kayanta ta bar gidan ta goma rugar su,wai tayi yaji, Wannan yajin da taji ba ta san ba karamin dadi yama mutanen wannan gidan ba, Ita a nata tunanin shine za'a biyo ta a bata haƙuri a kuma neme ta koma,ita kuma a lokacin zata wulakanta su, Abinda bata sani ba shine mutane da yawa a gidan ba su fatan ta dawo,dan haka kowa yayi banza da lamarin ta,aka cigaba da shagalin biki, Wasa_wasa sai da Amarya tayi shekara daya lokacin ta haihu tana da danyen goyo,sai gashi da rana tsaka Inna Binta ta tattaro kayanta ta dawo da kanta ba tare a anje biko ba, Wanda har yau Inna Mari na mata gori a kan haka,ta dawo gidan miji ba tare da yaje biko ba, Wannan dawowar da tayi,ta dawo ne da kwandunan bala'i a wannan lokacin,domin tsakar gidan Baffa Bube sai da ya kusan gagaran mutane shiga saboda kullun cikin yaƙi suke ita da Amaryar shi mai sune Hauwa, Yanda kasan ƴan daba haka suke,domin kuwa da zaran Inna Binta ta dauko Icce,Hauwa zata dauki katon muciya,ko ita ma ta dauki Faskare, Duk sun lalace sun zama kamar zararru, Su kenan kullum cikin zuwa asibiti dinkin goshi, Gaba ɗaya ta hana Hauwa zaman lafiya a gidan, Wani faɗa da suka yi wanda shine na karshe wanda ƴan uwan Hauwa suka dauke tare da kwashe kayan ta,wai ba zasu bari haka kurin a kashe masu yar uwa ba,ai kuma suka tafi da ita har da danta,dan cewa suka yi ba zasu bar matarsa Binta ta kashe shi ba,duk bala'in Baffa Bube dole ya bari suka tafi dashi,domin gaba da gabanta ne, Abinda ya faru kuwa shine, Akan abinci ne faɗa ya haɗa su,wanda dama ita Binta tana jiraye da ita,dan haka kuwa ta shammaceta ta saka muciya ta shemeta da shi,ai kuwa ta suma,domin ta bugu,kamar wasa ansa ruwa amma taki farkawa,wanda sai da aka haɗa da Asibiti,kwananta biyu sannan ta farfaɗo, Ganin ta farfado ne yasa yan uwanta suka yi hamdala, Daga nan suka dauki zuga su shida,uku yanninta mata uku matan yanninta maza,suka tafi har Rugansu Jauro, Kaman abin arziki suka ce sun zo daukar kayan Hauwa ne,babu wanda ya hana su tunda dama ita Inna Mari ba amfani gareta va,kuma Baffa Bube bai nan,dan shi kam yana son matar shi, Ita kuma Binta tana ganin haka ta hau shewa da cika bakin ta kori kishiya,har da kiɗa kwarya a tsakar gida, Hmmm,bata san dama da biyu suka zo ba,dan kuwa a ranar Binta ta yaba wa aya zakin sa, Domin babu zato babu tsammani suka rufe ta da duka ta ko ina,yanda ta nuna ma yar uwar su rashin imani haka suka mata, Domin sai da suka mata shegen duka sannan suka karya mata hannu daya da ƙafa ɗaya, suka bar ta nan kwance a sume,domin bata san in da kanta yake ba, Dukan mutum shida ba wasa ba, Makota naji ba wanda yayi ma tunanin ceton ta, Suna gama mata wannan ɗanyen aikin suka kwashe kayan Hauwa tas suka bar gidan, Ai kuwa wannan ciyon sai da ta shekara tana jinya kariya,domin abin bai zo mata da sauƙi ba, Wannan kenan. A lokacin Jauro yana shekaru goma sha bakwai a duniya,ya zama sauri sosai,domin yanzun duk abinda za'a mai dole a rage domin dai ƙarfin shi ya kawo,ta ɓangaren karatu kuwa ya sauke Kur'ani da jimawa wanda hakan ne yasa Malam liman ya saka shi hardar Kur'ani,kuma cikin nasara ya hardace, A Boko kuwa sai dai san barka,domin kuwa a wani gasa da makarantar su da suka je a Abuja ne ya ciyo masu na daya,wanda har a gidan TV an haska gasar, Anan Gamnati ta bashi scholarship na wani babban University a China in da zai yi karatun shekara huɗu, Wannan ci-gaban da ya samu a cikin gidan ba wanda ya damu dashi domin gani suke kamar aikin banza kawai zai tafi yi, Alhaji Abubakar Imam shi ne wanda ya tsaya mashi,yake kuma taimaka mashi akan batun tafiyar,domin kuwa shima babban danshi na can,a can yake karatu,tun last year, Dama kuma dashi yake son ya haɗa su, Acan Ruga kuwa,zaune suke a ƙofar gidan su Moha,su uku, Yana rike da wani dan littafi ƙarami na Turanci a hannun shi,suna hira yana dubawa lokaci lokaci, Sai su kuma da suke kallo a wayar Moha din shida yaron Malam Liman mai suna Musa, "Wai kai yaushe zaka siya waya ne Jauro,gashi tafiyarka bai wuce saura sati ɗaya ba" Cewar Moha. "Kyale ɗan iska ko da me yake son ya dinga kiranmu dashi oho,ba dai nufinka inka tafi shikenan sai ka dawo ba kuma,kar ka manta shekara huɗu suke ce,shekara huɗu ba kwana huɗu ba" Musa ya faɗa. Rufe littafin dake hannun shi yayi"ni ba zan iya riƙe abin ƴan iska ba,domin duk masu riƙe waya yan iska ne,kuma basu san amfanin kuɗi ba da zasu ɓata wurin sayan wannan abun" Zaro ido Moha yayi"ba dai mune ƴan iska ba Jauro? "Ka rantse babu abubuwan banza a cikin wannan wayar,karka manta Malam abinda na kamaka kana kallo a cikinta shekaran jiya,in ma aure kake so ai Gara ka yi magana kawai ayi maka" Ɗan dariya yayi yana shafa keya dan yasan bai da gaskiya,"to amma duk da haka ya kamata ka siya waya ko dan ƴan uwa" Kallon mamaki yake mai"ƴan uwa?ƴan uwa fa kace?ni ina da wasu ƴan uwan da zan kira ne ko su kira ni,?ai in dai ma zan siya waya sai dan mutum uku,dan in ji muryar Malam liman,sai kai sai kuma Alhaji,yana nufin Alhaji Abubakar Imam, Dan ku kawai zan iya siyan waya,to ku din ma ba zan siya ba dan ban iya amfani da ita ba,amma na dinga aron na ɗan Alhaji ina kira in ji muryar ku" Tsaki Musa ya ja "ɗan ƙauye dai duk yanda akayi dashi sai ya nuna halin shi,ɗan Allah Jauro kar ka bada mu,yanzun fa babban yaro zaka koma,ka zama ɗan gayu,amma ka tsaya kana magana kamar irin wanda bai taɓa shiga aji ba,kai ko dan irin sha'awan nan ba kaji,kalli yaran makarantar ku,kowa ka gani da babban wayar shi yana yanga,daga mata har maza amma kai kullun cikin riƙe takarda kake," "Ai duk yan iska ne,ni kaga kar ka ishe ni da batun waya,domin ni a nawa ganin duk masu rike waya basu da aikin yi,na biyu kuma iskanci suke kallo a waya kamar dai ku" "Oh mun shiga uku da Jauro,wai kai an ce maka duka ne aka taru aka zama daya,yanzun fa zamani ya canja,kuma zaka ce na faɗa maka da kanka zaka zo ka siya waya," Mikewa yayi tsaye "Allah ya raba ni,ni dai ku shirya min tsaraba kunsan ran sati ne rafiyar mu" "Ni dai me kake son in siya maka" Cewar Musa. "Naga Innar ka tana shanya kanzon tuwo,shi zaka karba min,sai ka haɗa min Sugar da Kuli-kuli,kai kuma Moha Garin Rogo da suyayyen gyaɗa,sai kwalin Lipton,sauran siyayyan in naje can na karasa," Baki buɗe Moha ke kallon shi,yayin da ya juya ya wuce abin shi yana ce masu sai sun haɗu anjima a wurin Malam liman, Juyo da kallon shi gun Musa yayi,tare da nuna Jauro da yatsa"anya yana da hankali kuwa? "Me yayi? Domin shi Musa bai yi karatu ba. "China ne zai je da kanzon tuwo,har da gari,kodai ya ɗauka boarding school za shi ne? " Au ba'a zuwa da su? Tsaki ya ja shima ya tashi tare da bar mashi wurin dan ba zai iya da wannan haukan nasu ba,tsakanin Jauro da Musa bai masan wanda yafi wani hauka ba..... *🍂JAURO🍂* (MAI ANGUWA) Story & Writing By JIDDARH UMAR 🌟🌙🌙🌙🌙🌙🌙🌟 *🌙✨MOONLIGHT WRITER'S ASSOCIATION🌙✨* https://m.facebook.com/Moonlight-writers-association-109698351308376/ *'''We are the moonlight writers we shine all over the world.''🌍'* ✍️✍️ بِسم الله الرحمن الرحيم ~~~~~~~💞💞~~~~~~~ *Ban yarda wani ko wata su saka min littafi a shafin su ko su mai da min littafi Audio ba tare da izini na ba* *16* *Wannan littafin nawa mai suna a sama na mai da shi na kuɗi,tare da Yar Tsanar Zinare,wanda yake son guda ɗaya dari uku 300,guda biyu 500 dari biyar, Hauwa Umar,Zenith Bank,2284905309,sai shaidar biyi ta wannan number 08141644865* A ranar da zai bar Minna zuwa Abuja ne ya je ya same Baffa Bube ya tsugunna a gaban shi"Baffa zan tafi makaranta " Kallon shi yayi daga sama har kasa,takalmi silifas ne a ƙafar shi,sai wasu kodaddun kaya riga da wando na yadi a jikin shi,duk yayi wani kura_kura dashi yanda kasan Almajirin ƙauye,ko ɗan mai bai shafaba,to ina ma ya ganshi balle ya shafa, Bushewa yayi da dariya harda nuna shi"yanzun kai Jauro a haka kake faɗin zaka kasar turawa karatu,ni kan anya mutumin nan ba dan yankan kai ba ne?in ba haka ba ta yaya zai ce zai kai ka kasar turawa wanda sai an shiga jirgi,sannan ace bai amsa ko sisi ba daga wurin mu,? Shiru yayi kawai yana kallon kanin mahaifin na shi, "To ba damuwa tashi ka tafi,idan kana da rabon dawowa Allah ya sadamu da Alkhairi,idan kuma Allah bai yi zamu kara ganin ka ba,to ka gaida mahaifinka sai mun iso,ka ce ya ajiye mana wuri zama mai kyau kar ya bari a cike wuri" Yama rasa mai zai ce mashi,dan haka tashi yayi kawai ya fito tare da shiga shiyan Baffa Sanda,in da yake zaune shi kuma yana wasa Addan shi, Tsugunnawa yayi shi ma a gaban shi "Baffa zan tafi makarantaba sai dai Allah ya dawo da mu" Bai bar abinda yake ba sai kallon shi da yayi"ina ne ma kace min zaka karatun duniya " "Baffa China na" "Ohh,to kai dai ka san su,kai da waye zaka tafi? " Ni kaɗai ne,amma akwai yaron Alhaji a can tare dashi za mu yi karatun" "To madallah,idan dai kaje ka ga zasu cuceka ka gudo ka dawo gida,kar ka yarda su sayar da kai,dan wani aboki na ya faɗa min idan sun ga ba kaɗa wayau,tsaf zasu siyeka su baka kuɗin ka cinye,daga baya su zo su tafi da kai su yanka bayan ka gama tara maiko, Dan haka kayi hankali dasu,banda kallon mata masu tafiya tsirara jauro,dan kana iya makancewa" Jikin shi ne yayi sanyi da huɗubar Baffan na shi,to yanzun idan yaje aka siye shi aka bashi kudin shi ya cinye fa,gaskiya da an samu matsala,dan aradu ba zai yarda yana ji yana gani ya tsaya a yanka shiba,gashi yaji ance harda Naman gwangwani suke yi, Wani tsoro ne ya kama shi,tare da haɗiye yawon tsoro,shi tsoro ma ya kama shi,sai dai kuma ba halin yace ya fasa"insha Allah Baffa," Ajiye Addan yayi a gefe ya saka hannu a Aljihu ya ciro ƴan dubu dai_daya a Aljihun shi tare da wasu canji, Jujjuya kuɗin yayi,ya buɗe su,sai da ya kirga su da kyau dubu Arba'in da huɗu ne da dari biyar,sai canjin Naira Saba'in a sama wanda suke Naira ishirin_ishirin guda uku naira goma guda ɗaya, Canjin saman ya mika mashi wato Naira saba'in ɗin tare da maida sauran kuɗin Aljihun shi"karɓi wannan kasha ruwa a hanya" Amsa yayi yana ɗan bata fuska,dan ya ɗauka zai bashi ko da dubu daya ne"na gode Baffa,"yana gama faɗar haka ya tashi ya wuce, Babu wanda ya mai rakiya koda nan da kofar gida ne, Sai dai Moha wanda shi ya kai shi har cikin gari gidan Alhaji Abubakar,in da yake jira sai yaga wucewar su Abuja kafin ya koma ruga *🍂JAURO🍂* (MAI ANGUWA) Story & Writing By JIDDARH UMAR 🌟🌙🌙🌙🌙🌙🌙🌟 *🌙✨MOONLIGHT WRITER'S ASSOCIATION🌙✨* https://m.facebook.com/Moonlight-writers-association-109698351308376/ *'''We are the moonlight writers we shine all over the world.''🌍'* ✍️✍️ بِسم الله الرحمن الرحيم ~~~~~~~💞💞~~~~~~~ *Ban yarda wani ko wata su saka min littafi a shafin su ko su mai da min littafi Audio ba tare da izini na ba* *17* *Wannan littafin nawa mai suna a sama na mai da shi na kuɗi,tare da Yar Tsanar Zinare,wanda yake son guda ɗaya dari uku 300,guda biyu 500 dari biyar, Hauwa Umar,Zenith Bank,2284905309,sai shaidar biyi ta wannan number 08141644865* Suna isa gidan har cikin falon Alhaji Abubakar Imam suka shiga da jagoran ɗan shi, Cikin girmamawa suka gaida shi suna zama a ƙasa, Amsawa yayi yana ƙare masu kallo, Yasan ko yace su zauna saman kushin ba zama zasu yi ba,wayar shi ya ɗauka yayi kira,wanda ko mintina biyar ba ayi ba sai ga ɗaya daga cikin yaran shi ya shigo, Nuna mashi Jauro yayi"ka bashi wasu kayan ya canja,kafin mu wuce" "Ok Dady" Ya bashi amsa,tare da juyowa wurin Jauro"taso mu je" Tashi yayi ya bi bayan shi suka fita, Dakin shi ya kai shi ya fito mashi da wasu riga da wando masu kyau,harma da takalmi,cikin farin ciki ya amsa kayan ya saka,irin wanda bai taba tunanin zai saka su nan kusa ba, Ya saka kaya kam,sai dai maganar gaskiya shine kayan basu wani yi mashi kyau ba,saboda kai da ka ganshi ba sai an faɗa maka ba kasan wannan duk yanda aka yi daga Ruga ya fito,shi ko dan irin wayewar nan da mutum zai nuna irin yayi karatu,to babu shi a tare da Jauro, Yana fitowa kallon shi ɗan Alhajin yayi tare da tabe baki,ba laifi kam,ba kamar dazu ba,kyara mashi kwalan riga yayi,sannan ya ja ahi suka koma falon inda su Moha suke, Koda suka shiga Alhajin baya falon sai Moha da aka kawo ma lafiyayyen abinci,ya ji nama manya-manya bai ciba yana jira Jauro ya zo suci, Suna shigowa kallon Jauron yayi yana sakin murmushi,"kai Jauro kayi kyau sosai,ka zama ɗan gaye," Shafa rigar yayi yana washe baki "baka ga ma takalmin ba,wani irin dashi,kalan na ƴan ƙwallo" "Gaskiya kaji daɗi sosai,matso mu ci abinci,gashi da zafin shi,zo ka gani" Matsowa yayi ya zauna yana kallon plate din dake gabansu, Nan suka zauna suka kwashi lafiyayyen abinci, Suna kammalawa yaron daya bashi kaya ne yazo ya kira shi wai ya fito zasu tafi in ji Alhaji, Sai da yaga zasu rabu da Moha ne ya fara hawaye,wanda sai da ya saka Moha din shima kuka,sai yake ganin kamar ba zai dowo ba, Sai da Alhaji yayi aikin lallashi kafin su hakura sannan ya shiga mota suka kama hanya, Har suka isa Abuja ko gyangyaɗa bai yi ba,yana kalle_kallen hanya, Sai da suka fara tsayawa a Hotel kafin zuwa ƙarfe huɗu su nufi Airport, Tashin hankali,domin kuwa sai da aka zo shiga jirgi yace bai san wannan ba,dan shi kam bai ga wurin shiga ba,balle ya shiga ya jeho shi kasa ya mutu,ba da shiba. Da kyar da lallashi da nasiha sannan Alhaji Abubakar tare da ma'aikatan jirgi suka samu suka shawo kanshi sannan ya amince,ba dan san ranshi ba,sai dan kawai yayi imani idan har ya mutu yau to lokacin shi ne yayi,kuma karin firgicin nashi ashe shi kaɗai zai je ba tare da Alhaji Abubakar ba,wai shi sai daga baya zai zo,idan ya je zai haɗu da Ɗan Alhaji da ke can, Masu aikin cikin jirgin wanda aka ba Alhakin kula dashi ne su suka sanya mashi belt din jirgi,su kuma suke ta ɗan kula dashi tare da kwantar mashi da hankali har zuwa sanda jirgin su ya sauka a China wuraren ƙarfe takwas na dare ne a garen. Daya daga cikin ma'aikatan jirgin da aka ba number Sadik ɗan Alhaji shi ya kira shi ya shaida masu sun sauka ya zo ya dauki ɗan uwansa,nan ya sanar dashi ai yana ma a cikin Airport ɗin, Tare da su ka fito in da anan suka hadu da wani matashin saurayi tsaye yana jiran su a wurin tarbon baki,dan haka yana ganin su da sauri ya zo ya rungume Jauro dan Dady ya turo mashi hoton shi, Godiya yama mutumin kafin ya fara dariya yana amsar jakkan dake hannun shi"barka da zuwa kasar China Abokina" Dan sanyi yaji jin ya mashi magana da yaren Hausa,"kai a gaskiya har naji daɗi da na samu mai jin yare na," Dariya ya kuma yi"ai ina jin yaren ka sosai tunda mahaifina Bahaushe ne,kaga taho mu shiga mota,ma karasa hiran a gida" Shi ya buɗe mashi gidan gaba ya shiga kafin ya maida kofar ya kulle sannan ya zagaya ya shiga mazaunin Direba ya ja muto, Shi dai kalle_kallen shi kawai yake yana baza ido yana kallen mutane masu wucewa,har suka isa wata unguwa mai kyau wanda tsarin gerin gidajen ma abin kallo ne, Har dakin daya tana da domin shi ya kaishi,tare da nuna mashi banɗaki da wurin wanka sannan ya fito"kayi wanka ka canja kaya sai kazo mu ci abinci" Amsa mashi yayi yana komawa banɗakin,dan ba karamin kashi yake ji ba tun cikin jirgi, To fa,tsayawa yayi yana karewa lafiyayyen bayin kallo,tare da shiga duniyar nazari, Dube_dube ya fara yi ko ta ina zai ga in da ake tsugunnawa,dan bayin a share yake tas,har wani kyalli yake,ko ina fari kamar daki, Idanun shi ne suka sauka akan wani dan net na roba,wanda idan ruwa ya zube a kasa yake bi ta wurin ya wuce,idan kuma datti yayi yawa a wurin ruwa baya wucewa,sai an cire roban an wanke, Dan haka ganin kaman dan rami ne a wurin yasa ya saka hannu ya cire roban yana leken ramin"kai gaskiya matsugunnin nan yayi karami,"ya faɗa yana kyara saitin tsugunnin shi a wurin, cikin kwanciyar hankali ya gama juye abinda ke cikin shi a wurin, Sai da ya kammala sannan ya dauki butan daya ciki da ruwa dama ya tsarkake jikin shi, Sauran ruwan da yayi tsarki da shine ya shiga juyewa a wurin,sai dai gani yayi abu ko motsi bai yi ba, "To shi kuma ta yaya zan saka ya wuce ce" Da sauri kuma ya juya tare da daukar bokitin wanka ya kunna panpo,sai da ya cika da ruwa ya jawo ya juye a wirin,sai dai a maimakon yaga ya wuce,sai gani yayi yama kara tasowa sama,bai da alamun sauka, Kara cika wani bokitin yayi ya juye,nan ma shiru babu labarin wucewar kashi, Shiru yayi tare da Daura hannayen shi duka biyu saman Kwankwaso yana tunanin ta yaya zai saka wannan kashin ya wuce ta ɗan wannan kwararon.... *Fans sai ku ba Jauro shawara* *🍂JAURO🍂* (MAI ANGUWA) Story & Writing By JIDDARH UMAR 🌟🌙🌙🌙🌙🌙🌙🌟 *🌙✨MOONLIGHT WRITER'S ASSOCIATION🌙✨* https://m.facebook.com/Moonlight-writers-association-109698351308376/ *'''We are the moonlight writers we shine all over the world.''🌍'* ✍️✍️ بِسم الله الرحمن الرحيم ~~~~~~~💞💞~~~~~~~ *Ban yarda wani ko wata su saka min littafi a shafin su ko su mai da min littafi Audio ba tare da izini na ba* *18* *Wannan littafin nawa mai suna a sama na mai da shi na kuɗi,tare da Yar Tsanar Zinare,wanda yake son guda ɗaya dari uku 300,guda biyu 500 dari biyar, Hauwa Umar,Zenith Bank,2284905309,sai shaidar biyi ta wannan number 08141644865* Shikam yasan ba shida zaɓi daya wuce yaje ya nasar da ɗan Alhaji ya zo ya taimaka mashi su saka wannan najasar wucewa,dan haka fitowa yayi daga cikin daki ya shiga ƙwanƙwasa mashi kofar dakin shi, Fitowa yayi "lafiya Jauro,kana buƙatar wani abu ne? " Ɗan Alhaji nayi bahaya kuma yaki tafiya sai yawo yake saman ruwa" "To muje na nuna maka yanda zaka yi" Bin bayan shi yayi suka shiga cikin dakin shi,tun daga shiga ban ɗakin wari ya fara busu shi,yana buɗe bayin ya dawo baya da sauri yana dariya tare da jawo kofar, "Ai Jauro yaushe aka ce maka anan ake bahayar," "To yanzun ya zan yi ɗan Alhaji?dan shi sam tunanin shi bai bashi cewa akwai wani abu a bayin ba wanda zai iya tsugunnawa a kai ba,dan shi kam tunda yake a rayuwar shi bai taba ganin ban ɗaki haka ba. " Zo muje bandaki na na nuna maka yanda zaka gyara naka" Bin bayan shi yayi suka koma nashi dakin har banɗaki,nan ya shiga nuna mai asalin inda ake kashi da yanda ake kora ruwa ya wuce da yanda zai wanke bandakin da kuma yanda zai yi amfani da kayan wankewar dake jere acikin bayin har da ma na wanka,"yanzun kaje ka duba bayan ƙofar ka zaka ga abin shara da kuma abin kwashewa sai ka yi amfani dasu ka kyara bayin idan ka gama sai ka yi wanka" "To na gode Ɗan Alhaji" Fita yayi daga ɗakin ya koma nashi,yanda ya nuna mashi kuwa haka yayi,sosai ya wanke bayin ya kuma buɗe window bayan,yana kammalawa yayi wanka sannan ya canja kaya, A washegari da taimakon Ɗan Alhaji ya kammala komai na makarantar,sannan suka bashi umurnin fara daukar darasi a kowani lokacin a kuma bangaren daya zaɓa wato Pharmacy, Ba karamin farin ciki yayi ba, Sosai ya mai da hankalin shi akan karatun shi,da yake shi din mutum ne me ƙwaƙwalwa yasa komai yake zuwa mashi da sauƙi, Sai dai ta bangaren abinci wanda da farko ya so ya ɗan samu matsala saboda yawan ciye-ciye wanda yake jawo mashi zawo,sai da Ɗan Alhaji yayi da gaske kafin ya fara sassauta ma cikin shi, Rayuwar shi a wannan kasar ba karamin daɗi yake mai ba,domin babu abinda yake Missing daga gida ko mutanen gida, Sai dai lokaci-lokaci suna gaisawa da Alhaji Abubakar, Sai da yayi wata biyu kafin dan dole Ɗan Alhaji ya saka ya siya waya,wanda sai da kyar sannan ya iya sanin ma yanda ake amfani da ita,dan ko da ma idan sunyi waya da Alhaji Abubakar bai san ma ta yanda zai kashe kira ba, Da wannan sabuwar wayar ne yasa Alhaji Abubakar ya turo mashi number Moha,suka yi Vedio call harda ma Malam Liman, Da Moha ya buƙace ko ya kaima ƴan gidansu su gaisa ne,sai cewa yayi a'a ya bar su,dan yasan ko an kai masu ba abin arziƙi zasu faɗa mashi ba,to aciki wama zai ce aba. A hankali rayuwar shi ke tafiya a wannan ƙasar cikin nasara yayin da kwanaki ke tafiya zuwa shekaru,yana aji uku ne ɗan Alhaji ya kammala nashi karatun ya dawo gida,wanda da kyar suka rabu a wannan ranar dan ba karamin shakuwa suka yi ba, Dama kuma tun ɗan Alhaji na nan suke kasuwanci wanda suke turo kaya Nijeriya ana sai da masu,kuma yana aiki a wani babban shago wanda ake biyan shi, Da wannan kuɗin ne ya biya ma kanshi kudin shiga wata makaranta a England in da anan ya zaɓa domin yin master's degree din shi, Kuma Alhaji Abubakar bai hana shi ba ɗan ba karamin Alfahari yake da yaron ba,ya dauke shi tamkar ɗan shi, Rayuwar shi a England ne ya so ya sauya, Haduwar shi da wata yarinya mai suna Jesica,ita ta fara buɗe mai ido da kananun romance,wanda daga baya idanun shi suka buɗe, Sai dai in da Allah ya taimaka shine bai taɓa zina ba,duk yanda yakai ga romancing mace sai dai a tsaya anan, Yayi ƴan mata kala-kala wan da shi kanshi bai sai iyakarsu ba, Jauro mutum ne mai matukar wayau sosai,wanda duk wayou mace bata isa ta ci kuɗin shi ba,duk wani karairaya da zata mai,sai dai yace wani dare ne jemage bai gani ba,sai kuma idan shi yayi niyar baki, Ko da ya kammala karatun shi a England bai dawo gida ba,wata makarantar ya nima a Saudiya wacce ita wannan ta islamiya ce kuma karatun shekara biyu ne,hakan yasa ya karɓi aikin makarantar su ta dauke shi a England din,sai dai zai masu aiki ne a Branch din su dake Saudiyya, Zaman shi Saudiya yasa ya kara samun ilimin addini sosai,tare da shiriya,ya zama wani ustadz dashi, Duk tsayin shekarun da ya kwashe yana yawo a kasashe bai wuce a cikin wata huɗu yayi waya da su Baffa sau biyu ba, Amma Malam Liman kuwa har yasa an rushe gidan ahi an yi mai ginin zamani ba tare da ya bari mutanen gidansu sun sani ba,haka ma Moha yayi aure tun tuni domin har yana da ƴa,ba karamin Alkhairi yake samu a hannun Jauro ba ban bai manta dasu ba. Wasa_wasa sai da Jauro ya share shakara takwas a kasar waje,hudu a China biyu a England,biyu a Saudiyya, Ya tafi yana da shakara goma sha bakwai ya dawo yana da shekara ishirin da biyar, Ko da zai dawo sai da ya fara bin jirgin da zai sauka Dubai daga nan ya hau na Ethiopia,sai kuma wanda zai sauka a Abuja,sai da yayi kwana biyu a Abuja kafin ya shigo Minna domin a kwai wasu takardun da yayi Submitting, Ba karamin murna Alhaji Abubakar Imam yayi ba da ganin yanda yaron ya kara jirma da wayau,duk da lokaci lokaci yana kai mai ziyara, Sai dai kusan ta ɓangaren saka kaya babu abinda ya canja dan gane dashi, Baya son cire kuɗi ya siya kaya masu kyau na fitar raini ya saka,ya fi gane ya ta saka kaya kamar wanda ba shida shi,Alhalin kuɗin dake cikin asusun bankin shi Allah kaɗai yasan yawan su, Ko da zai shiga ruga bai je masu da wani kayan karya irin na azo a gani ba,dan wallahi yasan halin mutanen su, Tunda yana jin labarin komai a bakin wadanda yake waya dasu, Yayan Baffannin shi duk sun girma sun zama samari manya dasu,dan Yabbale da ɗan Fodiyo tuni sunyi aure har da yara, Amma sai dai abin mamaki babu abin daya canja dangane da zaman mutanen gidan,sai karo wulakanci da suka yi, Dan yanzun Ya'yan Baffa Sanda basu isa su bi ta gonar Baffa Bube ba su wuce,kamar yanda shima ya'yan shi basu isa subi ta cikin gonaki Baffa Sanda ba. Inna Mari tsufa ya ƙara kamata sosai,sai dai in da Allah ya taimaka kunsan jikin Fulani da kyau,tunda yawanci da danyen madara suke fara karin safe, Basu wani damu da dawowar shi ba sai ma cewa da suke wai ya gaji da yawon duniyar da ya tafi ya dawo, Su Moha ne da ƴan gidan su Malam Liman kawai suka yi farin cikin ganin shi,wanda Malam Liman harda hawayen daɗi, Kwanan shi biyu da dawowa ya samu kira daga Abuja wanda yasa dole ya tattara yatafi, In da ya samu labari mai daɗi,a kan ya samu aiki a wani babban general Hospital na Gwagwalada,sun bashi babban matsayi a Lab din, Sai kuma aikin safaran Condom wanda wannan contract ne daga World Health Organization (WHO) ya samu, Sannan daga baya kuma ya fara aiki a nan general Hospital Minna, In takai ce maku masu karatu,a shakara ɗayan da dawowar Jauro,ya nada manyan gidan kifi wanda kifi kawai ake kiyo da kaji masu zaman kansu har guda biyu anan cikin garin Minna,sai ɗaya a Abuja, Jauro nada Babban Pharmacy wanda babu abin da ake siyarwa a ciki banda magunguna,ma'aikatan da ke aiki a wurin sunkai mutun goma da yan safe daban yan yamma daban, Yana da daya a Kaduna. Sai kuma mashina da yake rabawa matasa haya wanda wannan aikin ya bar ma ɗan Alhaji ne,shi dai nashi sai dai yayi order,gashi ko wani wata yana karbar Albashi mai matukar tsoka daga gwamnati, A taikaice masu karatu jauro yana da kudin da shi kan shi bai san yanda zai yi dasu ba, Abinda zai baka mamaki shine zaman da yake yi a nan cikin gari ba zaman aiki bane kawai domin Jauro harda noma yake yi,idan damuna ta sauka,ta can cikin unguwar ya siya wani tafkeken fili anan yake noma shida ma'aikatan da ya dauki haya, Shi bai yarda da wani abuba wai shi rayuwar karya,inaaa ba dashi ba,ya sha wahala ya tara kuɗi sannan ya ta kashewa,gani yake asara ne, Jauro yayi Dating ƴan mata da yawa dawowar shi,sai dai makonshi ke sa su rabu dashi, Yana iya ɗaukar budurwa yanzun ya kai ta Restaurant cin abinci,da sun isa zai jawo mata kujera yace ta zauna bari yaje ya masu order, Yana zuwa farko abinda zai tambaye su shine menene ya kare a wurin,ma'ana shine wani kalan abinci ne suka san ba su da shi, Idan sun faɗa mai sai ya koma wurin budurwar yana yamutse fuska,sai yace mata ai da naso mu ci bu kaza ne amma sunce basu da shi,tashi kawai muje wani wurin, Idan me hankali ce sai tace to ya siya masu drinks susha,idan kuma mai wayau ce sai ta bishi suje wani wuri,wanda nan ma suna zuwa ko dai ya ƙara mata haka,ko kuma yace ai sun ce Nama ya kare,ko kuma babu Kifi,dole dai karshi a bige da shan drink, Kuma duk bala'in ki bai bari ki ga Menu balle ki zaɓa. Shi yasa yawancin mutane suke masa kallon wanda bai san abinda yake yi ba,kuma matalauci, Wannan shine asalin Jauro, To masu karatu,ko yaya zata kaya tsakanin Jauro da Sumayya, Ko zata iya cin kuɗin shi, Ta yaya ya haɗu da mahaifinta har ya amince mashi, Zata aure shi kuwa, Yaya Ahalinshi,ya zasu ƙare, Ya labarin dukiyar shi na shanaye da aka tafi dasu,shin zasu cika Alkawari su dawo mashi dasu. *🍂JAURO🍂* (MAI ANGUWA) Story & Writing By JIDDARH UMAR 🌟🌙🌙🌙🌙🌙🌙🌟 *🌙✨MOONLIGHT WRITER'S ASSOCIATION🌙✨* https://m.facebook.com/Moonlight-writers-association-109698351308376/ *'''We are the moonlight writers we shine all over the world.''🌍'* ✍️✍️ بِسم الله الرحمن الرحيم ~~~~~~~💞💞~~~~~~~ *Ban yarda wani ko wata su saka min littafi a shafin su ko su mai da min littafi Audio ba tare da izini na ba* *19* *Wannan littafin na kuɗi ne 300,ga mai buƙata ya turo ta wannan asusun Hauwa Umar, Zenith Bank, 2284905309.* Abinda ya faru kuwa da su shine,yaran Baffa Sanda ne zasu tafi kiyo wato kannen su Yabbale,da Dotti da Nura, sai suka biyo ta gonar Baffa Bube,anan suka sami yaran shi da nasu dabbobin suna hutawa,ita kuma Binta tana ɗiban kara wanda zata je tayi girki dashi, Kokarin biyowa ta cikin gonar suke su wuce saboda hanyan zai fi masu sauƙi akan suyi zagaye, Ganin sun shigo masu ta cikin gona ne yasa da sauri kanin Ɗan Fodiyo wanda bai wuce shekaru goma sha ɗaya ba ya taso ya tsaya a gaban su,cikin rashin mutumci yace basu isa subi ta cikin gonarsu su wuce ba,bancin kuma ko a girma Dottiya ma ya girma yayanshi na biyu wato Ɗan Fodiyo, Kallon yaron yayi yace masa ya matsa masu mana bai da kunya ne ai wucewa kawai zasu yi, Cikin rashin da'a yace ko da ace Baffa Sanda ne zai zo da kanshi yace zai wuce ta cikin gonar nan ba zasu bari ya wuce ba balle su, Wannan maganar da yaron yayi ne ya tunzura Dottiya har ya daga hannun ya mashi mari mai lafiya, Shi kuwa jin zafin marin ne yasa ya faɗi ƙasa yana ihu, Jin ihun ɗanta ne yasa Binta bata jira komai ba kuma bata nime bayanin komai ba ita dai kawai taga su Dottiya tsaye kan ɗan ta,dan haka sanda ta dauka lafiyayye ta zagayo ta bayan Dotti wanda ba zato ba sammani yaji saukar sanda a kanshi, Shi kuma jin zafin hakan ne yasa cikin zafin rai ya kawo sara ta bayan shi ba tare daya san wanda ya mai wannan aikin ba, Ita kuma da yake Allah ya kiyaye sai ta tare saran da hannun ta,wanda saran ba karamin shiga yayi ba dan har ana ganin kashin hannu, Wannan shine musabbabin komai domin kuwa yaranta manya tasowa suka yi suka ce basu yarda ba,dole kuma sai sun daukar ma uwar su fansa, Bayan kwana biyu da faruwan haka ne ranar Jauro ya shigo ƙauye,shine Bakari ɗan Binta na farko ya tare shi,wai yaga Alama yanzun wani tashen rashin kunya yake ma mutane tunda yaga wasu yan kuɗi suna shigo mai,dan haka yayi hankali da su, To shi bai ma san wani rashin kunyar yake masu ba, To kwana uku da wannan maganar ne shine ya shirya dan ya tafi ƙauye,Allah ya kiyaye shi bai isa ba ya dawo,to shine yake samun labarin kidnappen din Baffa Sanda da akayi tare da matarsa Kande, Wanda dama kuma an daɗe da fara zargin su Ɗan Fodiyo da irin wannan harkar, *CIGABAN LABARI* A jiyar zuciya ya sauke mai ƙarfi yana gyara kwanciyar shi,gara ya bari washegari da rana kawai ya shiga ƙauye, ______ɓangaren Sumayya kuwa,tunda ta kammala girkin rana take jiran dawowar Mama,sai dai shiru har kusan ƙarfe uku na rana sai gashi ta dawo, Buta ta dauka ta zaga bayi,tana fitowa ta daura Alwallah ta shige daki, Ita kuma ganin ta dawo ne yasa ta bi ta ɗaki ta samu wuri ta zauna tana jira ta idar. Jira kawai tayi ta sallame sallah ko tasbihi bata yi ba,ta matso gabanta ta zauna tana zuba mata ido"Mama kin je?me ya ce ? Za'a fa... Hannu ta daga mata,tana tasbihi da hannu,sai da tayi goma sannan tace"ai dai kya bari na numfasa ko" Bata fuska tayi"dan Allah Mama ki faɗa min,wallahi hankali na ya kasa kwanciya " Cire hijabi tayi tana mike ƙafa "banje ba" Zaro ido tayi "Mama! " Eh banje ba,ina fita na haɗu da malama Sadiya,Babban malamar islamiyarmu,ita na bi gida,tun dazu ina gidan ta,kuma na faɗa mata duk abinda ke faruwa,dan haka tace na faɗa maki ki zo gida ki same ta,kuma karna kuskura naje gidan wani malami,dan zan bata imani na ne,dan haka anjima sai ki shirya ki je gidan ta" Cikin jin haushi tace"Uwar me zan mata a gida,ni ba inda zan je " Buge mata baki Mama tayi"kina da hankali kuwa? Kuka ta fashe da shi,"ni wallahi ba inda zan je,muguwar mata kawai," Ganin Mama na niman abun bugu ne yasa da sauri ta tashi ta fita dakin tana kuka, Shi kenan ta shiga uku yanzun ina zata samu mafita, Tunda ta shige daki take kwance tana kuka,har aka idar da sallar la'asar,sai da Mama ta shigo ta ci mata mutunci sannan ta fito tayi Alwallah tayi sallar, Tana zaune kan Darduma tana jan carbiw wani tunani ya fado mata,dakatawa tayi da jan carbin tana nazari abinda ya fado mata a zuciya, Dan haka cikin sauri ta Mike tsaye tare da kwabe hijabinta ta canja wani,ko kwalliya bata tsaya yi ba ta fito, Dakin Mama ta leka wacce ke zaune tana cin abinci "Mama na tafi gidan Maman Momy" Dagowa tayi ta kalle ta"me zaki je yi a can? "Kawai dai zan je gaishe ta ne" Kallon sama da ƙasa tai mata"ke ɗin ce a yau zaki je gaishe ta? Turo baki tayi"eh" "To ba zaki ba,dan bana son fitina,baki je bama ance kin je kinyi balle kuma kin je,ko ma ki zauna" Bubbuga kafa ta fara kamar karamar yarinya,domin Sumayya irin yaran nan ne da Allah yayi su da fitina da kafiya "ni Mama zuwa kawai zan yi in dawo,kuma ba fitina zanje yi ba," Kauda kai tayi tana ci gaba da cin abincinta kamar bata san da ita ba, Ganin Mama ta ƙyale ta ne yasa ta sadada ta fita gidan da sauri, tana tare mai mashin ta hau tace ya sauke ta ƙarshen layin su,duk da ba tafiya bane mai nisa ko da kafa zata taka,amma gudun Mama ta aika a dubata yasa ta hau mashin, A bakin kofar wani gida mai bakin Get lafiyayyen ta sauka ta mika ma mai mashin Naira hamsin. Maimakon ta shiga gidan sai tsayawa tayi tana karewa Get din kallo cikin mamaki kuma lokaci guda tana hararan Get ɗin gidan kamar shi ya mata laifi, Kafin ta isa bakin kofa ta tura ta shiga, A tsakar gida ta samu matar gidan tana wanki wacce jin an buɗe Get an shigo ne yasa ta ɗaga kai tana kallon ta cikin mamakin wacce ta gani, Ita kuma ganin wacce ke tsakar gidan ne yasa kuma taji kamar ta koma,ta fasa yin abinda ya kawo ta,sai tsaki take ja a zuciyar ta, Kallon yanda take wani har haɗe fuska matar tayi,lokaci guda kuma ta saki wankin da take tana murmushi wanda kai da gani kasan ba da zuciya daya take ba,ta kama hanci ta sake wani irin guda mai sauti tare da saka dariya tana riƙe haba "ah yau amarya ce a gidan nawa,lallai aure mai saka hankali" Bata ce mata komai ba ta jawo kujeran dake gefe ta zauna, Kamar ba zata mata magana ba tana turo baki tace"ina wuni" Tsakar kanta ta tsaya ta ƙara rangada wani budar "Lallai yau Allah na gode maka daka nuna min ranar dani Sumayya zata gaida ni,Allah kasa ba mutuwa na kusa ba" Sai da ta Harare ta kafin tace"nifa Maman Momy ba faɗa na zo ba,kawai dai nazo ne na rokeki akan kisa Baba ya fasa wannan auren domin nasan maganar ki kaɗai yake ji" "Eye,eye,lallai,wato ma kinsan magana ta kadai yake ji,to me zai hana ki ce Uwar taki ta kwada nata sa'ar akan shi" "Ni dai na fada maki ba faɗa ya kawo ni ba" "Eh dole ki ce haka tunda laluran gaban ki ne ya kawo ki ba,to bari ki ji ba zan faɗa mashi ba,domin kuwa aure ke da wannan bakin baƙauyen babu fashi,ai na faɗa maki,sai na lalata rayuwar ki,sai na mai dake abin tausayi fiye da Uwar ki,ke bari ma na fada maki abinda baki sani ba,ni na haɗa babanki da Jauro,na kuma zuga shi akan ya aura mashi ke,na ce ya faɗa mashi kuna idan ya aure ki kar ya kuskura ya bari ki yi aiki,ba dai takamarki kinyi karatu zaki nime aiki ki taimata ma Uwar ki ba,to babu batun aiki a rayuwar ki,sai dai ki zauna a ƙauye tare da fitinannun ƴan uwan shi waɗanda ko tashin hankalin su ya ishe rayuwar ki" Ji tayi ranta ya baci,hankalin ta ya ƙara tashi "wato ke kika zuga Baba akan haka ba? Lallai ke muguwar ce Lami,me yasa baki ba shi Jauro auren yarki Momy ba sai ni,me na tsare maki,me muka miki? Dariya ta kuma sawa" Ai cewa kika yi yata,ta ya za'a yi na zaɓa ma yata irin wannan mutumin da bai san Me yake yi ba,ki bari kiga irin mijin da Momy zata aura,sai kun koma kuma masa maula ke da Uwar ki harma dashi mijin naki,kuma bancin haka me amfanin ɗan kishiya" Mikewa tsaye tayi"in Allah ya yarda burin ki ba zai taba cika akan mu ba"tana faɗar haka ta bar gidan tare da bugo Get, Juyowa tayi ta kalle Get din hawaye na zuba a idonta,a zahirin tace"Baba baka da adalci"ta faɗa tana juyawa tana tafiya a hankali tana ɗan goge hawayen idon ta,wannan matar Baban nasu makira ce,muguwa,kuma Azzaluma,dubi gidan da Baba ya gina mata ita da yaranta biyu,amma su ya bar su a tsohon gida da ko ƙofa babu, Juya baban su take kamar waina sai yanda tayi dashi,Mamar su ba tada katabus, Wlh wata rana suna sati ɗaya ma basu ganshi ba,alhalin suna unguwa daya, Wato ita ke kara zuga Baba yana masu hauka,, ko ina kuma ta san Jauro oho,in Allah ya yarda sai ta ga abin ta. *Last free page* *🍂JAURO🍂* (MAI ANGUWA) Story & Writing By JIDDARH UMAR 🌟🌙🌙🌙🌙🌙🌙🌟 *🌙✨MOONLIGHT WRITER'S ASSOCIATION🌙✨* https://m.facebook.com/Moonlight-writers-association-109698351308376/ *'''We are the moonlight writers we shine all over the world.''🌍'* ✍️✍️ بِسم الله الرحمن الرحيم ~~~~~~~💞💞~~~~~~~ *Ban yarda wani ko wata su saka min littafi a shafin su ko su mai da min littafi Audio ba tare da izini na ba* *20* *Wannan littafin nawa mai suna a sama na mai da shi na kuɗi,tare da Yar Tsanar Zinare,wanda yake son guda ɗaya dari uku 300,guda biyu 500 dari biyar, Hauwa Umar,Zenith Bank,2284905309,sai shaidar biyi ta wannan number 08141644865* A hankali take tafiya kamar wacce kwai ya fashema a jiki,tsabar yanda jikinn ta yayi sanyi,bata damu data hau mashin ba wannan karon da kafa ta taka har gida, Bata ma nime Mama ba ɗakinta ta shige,dan ta san ba tada wani hujjar da zai saka ta nime ta tunda ta hanata zuwa, Ganin in ta zauna tunani yana iya sakawa zuciyarta ya buga ne yasa kawai ta tashi ta kwaso kayan da aka ci abinci ta shiga wankewa, A takaice ko mintina goma sha biyar bata gama haɗawa ba da dawowa sai ga Baba ya shigo cikin bacin rai wanda ko sallamar bai yi ba, Sai ma kwala kiran sunan Mama da yake kamar zai tada gidan, A razane ta fito daga ɗaki dan barci take yi, Tsayawa tayi a gefen shi "Baban Aisha gani" Nuna ta yayi da ɗan yatsar"wato baki da mutunci ko Hajara,yanzun har yakai kina koyawa ya'yan ki rashin tarbiya,abun ya tashi daga kaina ya koma kan matata kuma" Jin ya ambaci sunan matar shi ce yasa ta juya ta kalli inda Sumayya ke zaune,wacce ko juyowa in da suke bata yi ba,asalima kamar bata jinsu sai cigaba da wanke-wanken ta da take yi, "Baban Aisha wallahi ban aika kowa gidan ba" "Ai dama haka zaki ce mara mutunci,ita kuma Sumayya da kika aika taje ta zageta tas,har da kiran min mata munafuka,da zagar mata iyaye,yanzun ke Hajara ba abin Alfahari bane ace kishiyar ki ta zabarma ƴar ki miji,amma da yake baku gode Allah shi yasa" "Kayi haƙuri Baban Aisha,kaima kasan tunda na rokeka ka ki,shi kenan na fita batun wannan maganar,ni dai addu'a ta shine inda Alkhairi a wannan aure Allah ya tabbatar,in kuma baba Allah ya zaɓa mata wanda yafi shi" "Ai gara ki daina wahalar da kanki,domin aure kamar anyi an gama ko da kuwa babu Alkhairi" Tama rasa mai zata ce mashe tsabar takaici,wanda kuma bana kowa bane face na Sumayya,duk ita taja mata,inda ace bata je gidan ba ai da bai zo ya mata wulaƙanci ba, Juyowa tayi ta kalle shi"to Baba mai zai hana ka dauki Momy ka bashi ya aura tunda ni bana so,ai naga ita ma ta isa aure,amma tsabar san kai sai ace ni za'a ma dole sai kace zamanin da" Cab,lallai Sumayya ta taro march,Bokitin dake gaban shi yayi ƙwallo dashi"ni kike faɗa ma haka,Sumayya ni mahaifin ki kike ma rashin tarbiya,na tabbatar da Momy ne daga bata min haka ba,shi yasa ko yaushe kuke a tambade kuda Uwar ku," "Baba ni fa ban faɗa wani abu ba kawai dai auren ne bana so,na amince kai ka zaɓar min wani mijin da kanka amma ba wannan matar ba" "Ina magana kina magana,Sumayya Allah ya tsine maki Albarka daga ke har uwarki dake daure maki gindi,kuma in dai ina zaye zabin Maman Momy shine zaɓi na,shi zaki aura koda a ce ana kaiki zaisa wuƙa ya daddatsaki yayi gunduwa gunduwa dake,to bari ki ji ni zan tsaya mashi a ƙoto dan kar a daure shi domin annoba ya kashe ya ragimemin mugun iri a zuri'a ta" Wadannan maganganun da yake faɗa su suka tunzura Mama suka kona mata zuciya har ta shiga mai da masa da martani ita ma cikin zafin rai "Sumayya! Sumayya! Sumayya! Yanda na kira sunan ki sau uku Allah ya miki Albarka,ya aibarkaci rayuwar ki,in Allah ya yarda ba zaki taɓa tabewa ba,sai kin zama abin Alfahari a gidan nan" Juyowa tayi kanshi "bakinka ba zai taba kama yata ba tunda dai bata hakkin ka,me ta maka da zaka tsine mata,duk bakin cikin da kake kuntsa min mai ishe ka ba sai ka koma tsine ma ya'ya na,to bari kaji tsinuwarka ba zai taba kama su ba sai dai ya sauka akan waɗancan ƴan gold din ba baka ganin laifin su,kuma sai Allah ya saka mana,munafiki" Ganin yanda ita ma ta taso masa ne yasa cikin bacin rai ya juya ya bar gidan yana faɗin "ko kunki ko kunso aure babu fashi,na ma maida shi cikin wannan wata,sai dai tasha fiya_fiya ta mutu" Daga inda take zaune ta fashe da kuka tana haɗa kai da guiwa "shi kenan na shiga uku rayuwata tazo karshe tunda mahaifina yamin baki ya tsine min" "Kul na kuma jin kiyi kuka akan haka,ba abinda tsinuwarshi zai maki,yanzun zan je wurin yayanshi duk yanda za'ayi dole ayita ta kare,domin na gaji da wulakanci da matar nan ke ja min" Ku yi haƙuri ba yawa *🍂JAURO🍂* (MAI ANGUWA) Story & Writing By JIDDARH UMAR 🌟🌙🌙🌙🌙🌙🌙🌟 *🌙✨MOONLIGHT WRITER'S ASSOCIATION🌙✨* https://m.facebook.com/Moonlight-writers-association-109698351308376/ *'''We are the moonlight writers we shine all over the world.''🌍'* ✍️✍️ بِسم الله الرحمن الرحيم ~~~~~~~💞💞~~~~~~~ *Ban yarda wani ko wata su saka min littafi a shafin su ko su mai da min littafi Audio ba tare da izini na ba* *21* *Wannan littafin nawa mai suna a sama na mai da shi na kuɗi,tare da Yar Tsanar Zinare,wanda yake son guda ɗaya dari uku 300,guda biyu 500 dari biyar, Hauwa Umar,Zenith Bank,2284905309,sai shaidar biyi ta wannan number 08141644865* Sai da tayi sallan la'asar sannan ta shirya ta tafi gidan Yayanshi wanda yake zaune a Sabon Anguwa, Sai dai cikin rashin sa'a koda ta je ta iske bayanan,dan haka ta samu uwar gidan shi ta faɗa mata komai tunda suna shiri ta kuma roƙeta akan dan Allah idan mijin ta ya dawo ta sanar dashi abinda ke faruwa,sannan tai mataa sallamah ta koma gida, Koda ya dawo matar sanar dashi tayi abinda ke faruwa,dan haka ɗaukar waya yayi ya kira kanin nashi akan ya zo tare da matanshi, Shi kuwa Baba daya tashi zuwa sai ya dauko Maman Momy kaɗai ya taho da ita a mashin din shi, A dakin da yake ganin baƙi suka same shi, bayan sun gaisa ne suka samu wuri suka zauna, Kallon shi yayan shi yayi"me gaskiyar maganar da matarka ta fada,sannan kuma me yasa ita Maman momy zata zaɓa ma Sumayya miji," Cikin sanin makamar kissa ta fashe da kuka"yaya tsakani da Allah nake zaune da mijina da kuma ya'yanshi, ban taɓa yin wani abu domin na cutar dasu ba koda matar shi,amma ita ko yaushe cikin bina da sharri take yi,bana bi ta nata domin duk abinda nasan zai amfanar ita da ya'yan ta shi nake yi, Jauro mutumin kirki ne,yaro ne mai hankali Yaya,domin idan bana kwarai bane bazan taba zaɓar ma Sumayya shi ba,ka yarda da ni,kuma shi kanshi mahaifin nata yayi bincike akan shi,na tabbatar da ace yaga da cutarwa ai ba zai yarda ba Yaya" Ajiyar zuciya ya sauke "da gaske kayi bincike a kan mutumin? Ya faɗa yana kallon Baba " Na yi bincike akan yaron sosai,kamar yanda ta faɗa " "Yaya ina da magana kuma,ɗan Allah ka taimake ni ka shiga wannan lamarin" Ta faɗa tana kara ƙarfin kukanta harda gudun hawayenta, Shi kuma Baba sai wani lallashinta yake yi, "Ina jinki," Faace majina tayi da kyallen dake hanunta,"wata uku da suka wuce naje Asibiti likita ya tabbatar min da ina da ciyon hawan jini,ya ce ina bukatar wanda zai dinga kula dani yana taimaka min,in ba haka ba ina iya faɗuwa rabin jiki na ya shanye, Na roƙe Alfarmar maman Sumayya akan tabarmin Baban Momy har zuwa lokacin da zanji saki,da fari ta amince har yayi wata uku a wuri na,amma shine yanzun cikin satinnan har gida tazo ta sameni da cikin mutunci kan ita ta fasa barmin baban momy,wanda kuma Yaya shi yake taimaka min da wasu abubuwa da yawa,tunda kaga Momy na makaranta,shi kuma Sanusi ƙarami ne,shi kanshi yana buƙatar kulawa, Ɗan Allah ka taimake ni" Duk abinda take faɗi yana jinta tare da jinjina kai,"wata uku,to ke har yanzun ba kiji sauki ba ne? "Ko shekaran jiya munje Asibintin tare dashi an kuma auna jinin sai dai har yanzun bai sauka ba" "To shikenan kukan ya isa haka,zan mata magana,yanzun kai ka kira min ita ma na" "To yaya" Ya faɗa yana ciro waya a Aljihu ya kira number ta, Mintuna goma sha sai gata ta iso,matar gidan ce ta mata iso har inda suke, Tunda ta shiga taga yanda Yaya ya amsa mata gaisuwa tasan cewa akwai matsala, Bata ce masu kala ba sai zama da tayi a gefe,cikin kissa maman Momyi tace"Maman Sumayya sannu da zuwa" Bata kalle ta ba kuma bata ce mata Komai ba sai ma dauke kai data ƙara yi tana fuskantar Yaya, Wani irin farin ciki ne ya mamaye zuciyar ta wanda har saida ɗan murmushi ya nuna a fuskarta da sun lura,domin dama addu'a take akan Allah yasa karta amsa mata gaisuwa,domin zata iya ƙara samun ƙwarin gwiwa da rashin amsawar ta, Jinjina kai Yaya yayi,sannan ya kira sunan ta"naji bayani daga bakin Mijinki da kuma kishiyar ki,kuma na gamsu da bayanin su sosai,ɗan haka kuma ya yanke hukunci a kan abu na farko,shine Sumayya zata aure Jauro,batun girki kuma ita Maman momy zata cigaba da riƙe miji har taji sauƙi,domin ba tada mataimaki " Kallon mamaki take mashi"amma Yaya ta ya hakan zai kasance,wata uku da bai san cin mu ba balle shanmu,sai dai idan ya zagayo ya zo yaci wanda na dafa ma yara,idan nayi magana yace yanada mara lafiya,to ni da ya'ya na fa,Yaya ta ya taka faɗi haka ɗan Allah,ni ban damu da batun auren Sumayya ba,amma ni amin adalci," "Bana son wata magana ki bi umurni na kawai" Shiru tayi tana dukar da kai,wannan wani irin rashin Adalci ne,me yasa Yaya zai mata haka,bayan yasan tana jin kunyar shi,tana girmama shi,bata iya ci masa musu akan komai," Dago kai tayi"yaya ba komai Allah ya bata lafiya,sai dai ina rokon alfarma,ko da ba zai ba mu abinci ba,ina roƙon ka daka saka mana baki ya yafe ma Sumayya,ya kuma cire bakin da ya mata" Kallon shi yayi"bana son shashanci,me yasa zaka ma yarka baki,wannan ba halin ƙwarai bane,domin duk abinda ya'yan mu zasuyi wata ƙila idan aka duba tarihin rayuwarmu munyi abinda yafi nasu,kuma iyayen mu basu tsine mana ba,dan haka maza idan ka maida matarka gida kaje ka samu yarka ku dai-dai ta" "Insha Allah Yaya" "Ku tashi na sallame ku" Ta rigasu fita dan haka bata jira komai ba ta wuce gida,ko sallamar matan gidan bata yi ba,ta wuce, Allah ne kaɗai ya kai ta gida lafiya,tana isa kai tsaye ɗakinta ta shige ta kwanta tana turo ƙofa, Kuka ta fashe dashi tana kifa fuskarta acikin fulo,dan bata son ya'yanta su ji kukanta, Ji tayi an buɗe ƙofar an shigo an maida an kulle, da sauri ta dago kai tana share hawayenta, A hankali ta tako ta zauna a bikin gado tana dafa ta,tashi zaune tayi daga kwancen da take tana kakaro murmushin yaƙe,"me kike buƙata," Rungume ta tayi a jikinta "Mama is not bad for a parent to cry in front of their children,ki yi kukan ki,bazan hana ki ba,kuma bazan yi ba,ɓalle in rage maki kwarin gwiwa rage raɗaɗin dake zuciyar ki" Kamar jira take ta faɗa mata haka,nan kuwa ta fashe da kuka mai raɗaɗi tana ƙara rungumi Sumayya a jikin ta, Tayi kuka sosai wanda har saida taji wani sanyi yana ratsa zuciyar ta da nasuwa,wanda bana komai bane face na sumun kafadar da tayi kuka *🍂JAURO🍂* (MAI ANGUWA) Story & Writing By JIDDARH UMAR 🌟🌙🌙🌙🌙🌙🌙🌟 *🌙✨MOONLIGHT WRITER'S ASSOCIATION🌙✨* https://m.facebook.com/Moonlight-writers-association-109698351308376/ *'''We are the moonlight writers we shine all over the world.''🌍'* ✍️✍️ بِسم الله الرحمن الرحيم ~~~~~~~💞💞~~~~~~~ *Ban yarda wani ko wata su saka min littafi a shafin su ko su mai da min littafi Audio ba tare da izini na ba* *22* *Wannan littafin nawa mai suna a sama na mai da shi na kuɗi,tare da Yar Tsanar Zinare,wanda yake son guda ɗaya dari uku 300,guda biyu 500 dari biyar, Hauwa Umar,Zenith Bank,2284905309,sai shaidar biyi ta wannan number 08141644865* Sai da ta gaji dan kanta sannan ta dago tana goge idanunta da suka kunbura, Cikin sanyin jiki tace"Mama dan Allah ki yi haƙuri ki yafe min,laifina nane,idan da nasan abin zai kai haka da banje gidan ta ba,dan Allah ki yafe min kar kiyi fishi dani " Cikin shakakken muryarta wanda ya dushe da kuka tace"ba laifin ki bane Sumayya,nasan cewa dama kawai suke jira wanda zasu ci mutunci na,basu samu ba sai yanzun,amma babu komai haka Allah ya tsara min,a wasu lokutan da dama na kanji kamar na bar gidan mahaifin ku,na kama gaba na,saboda irin wulaƙancin da yake min na bayyane dana ɓoye,sai dai a duk sanda na kalle ku sai naji bazan iya tafiya na bar ku ba,saboda nina haife ku,na jure ko wani irin wahala tun daga na ɗaukar ciki har na raino,har kuka kai matakin da kuke a yau,sai dai har yanzun ban gama tarbiyantar da ku ba,akwai ƙananki ƙanana,idan na tafi wa zai kular min dasu,nasan ba a taɓa basu irin tarbiyan da nake masu kwaɗayin samu ba,wannan yana daya daga cikin dalilan dake kara sani in yi haƙuri, A da mahaifin ku ba haka yake ba,mutumin kirki ne,wanda nake girmamashi sosai kamar yanda yake girmama ni,ya nuna min soyayya da kulawa,har ma daku,ya shayar da ni daɗi dai_dai gwargwado,wata kila shi ya manta,amma ni ban manta ba Sumayya kuma ina son shi har yanzun" Rungume mahaifiyar ta tayi a jikin ta hawaye na zuba a idon ta"idan har ke mahaifiyar mu zaki iya sadaukar da farin cikin ki domin na mu rayuwar,mu a matsayin mu na ya'ya me zai hana mu sadaukar da namu farin cikin domin naku,Mama na Amince da auren Jauro,zan karɓe shi a matsayin miji,amma ba dan kowa ba sai dan ke mahaifiya ta" Dago ta tayi"A'a Sumayya,ada dai nayi niyar kibi zabin mahaifinki,amma yanzun kam ban yarda ba tunda matarsa ce ashe tayi zabin ba shi ba,ba zaki aure shi ba" Girgiza kai tayi"kar ki ce haka Mama,idan har ban amince ba komai na iya faru na sani kuma kema kin sani,bana son na kasance mai taurin kai a tsakanin ku,dan Allah ki cire komai a ranki kamar yanda nake kokarin yi yanzun," "Karki damu,yanzun zanje gidan matar kancila ta kai ni gidan wannan malamin,koma yaya ne ba za'ayi wannan auren ba" Share hawayen da suka zubo mata tayi"Mama dazu fa da kanki kika ce Malamar ku tace bai da kyau zuwa wurin malami,tabbas gaskiya ta faɗa maki,ni kan na haƙura,nayi imani da ƙaddara,domin Manzon Allah Sallallahu alaihi Wasallama yana cewa,idan zaka yi ruko,to ka roƙi Allah,haka kuma idan zaka ni me taimako,ka nime taimako a wurin Allah, To Mama me yasa ba zamu nime taimako a wurin Allah ba,a gani na yafi mana zuwa wurin wasu malamai waɗanda sai mu ɓata kuɗin motar mu domin zuwa wurin su,sannan kuma su karbi kudin mu,Amma kuma shi Allah a duk inda kake,ko da kuwa a cikin kabari ne,in dai har zaka yi addu'a Allah zai karɓa maka ba tare daka biya shi ba, Sannan yace (ka sani da za'a tare Al'umma domin su amfanar da kai da wani abu,ba zasu iya amfanar da kai komai ba sai abunda Allah ya rubutu maka, sannan yaci gaba da faɗin,Da za'a tara Al'umma domin su cutar da kai da wani abu,ba zasu iya cutar da kai da komai ba sai abunda Allah ya rubuta maka)na yarda da wannan hadisin, Nayi imani Maman Momy bata isa ta min abinda Allah bai min ba,ki kwantar da hankalin ki,bazan so saboda ni ki sauka a kan hanyar bin Allah ba,domin idan haka ta faru bazan taɓa yafe ma kaina ba" "Allah ya Albarkaci rayuwar ki Sumayya,idan har Allah yana karɓar addu'ar uwa a kan yarta,Ya Allah ina roƙon ka da kasa Albarka a rayuwar Ya ta,wannan auren idan har za'a yi shi da niyyar a tozarta mu ne,ya Allah ka saka albarka a cikin shi,kasa hanyar Arzikin sune,ka ba maƙiya kunya,Amin ya hayyu ya Kayyum" _______ɓangaren Jauro kuwa,sai washegari da rana tsaka ya shiga ƙauyen,dan Allah ya gani mugun tsoro gare shi,karma yayi sammako ya haɗu dasu a hanya,ko kuma yaje da dare wani abu ya faru dashi,shi yasa ya gwammace ya tafi da rana ido na ganin ido,, Ko da yaje ma ko awa biyu bai yi ba a cikin Rugan su ya fito,dan gaisuwa kawai da jage ya masu,sannan ya tafi gidan Malam Liman,shima yana ganin an idar da Sallar La'asar ya masu sallamah ya wuce, Koda mai mashin din da ya fito dashi daga cikin ruga ya ajiye shi,a maimakon ya samu ɗan adaidaita ya maida shi gida sai cewa yayi mai a daidaitan ya kaishi Barikin Sale,wanda wannan Anguwarsu Sumayya, Sam bai damu da yanda yayi butu butu da ƙura ra,saboda hanyar su ba kyau duk jar kasa tayi yawa,wanda yasa har ta suman kanshi ya canja kala zuwa ja, Sai ya koma yanda kasan wanda aka tono daga kabari, Sai dai shi ko a jikin shi, Har kusa da kofar gidan ya sauka sannan ya kara so da ƙafa,Allah yasa yana zuwa ya haɗu da Aisha zata shiga gida,dan haka tare ta yayi, "Kanwata zo in aike ki" Koda ta juyo ta haɗa ido dashi,sai ihu za saka tana sake ledan manja dake hannun ta na Hamsin wanda Mama ta aike ta,ta shige gida da gudu ta kiran a taimaketa ga mai yankan kai a kofar gida zai gudu da ita, Mama ce ta fito da sauri da ga banɗaki jin yanda yarinyar ta shigo a gigice, Tambayarta tayi lafiya meke faruwa, Sumayya ce ta faɗa mata wacce ke rike da Aisha a jikin ta, "Je ki wurin Mama bari in duba ko waye" "Duba,kinsan halin Aisha da tsoro"... *🍂JAURO🍂* (MAI ANGUWA) Story & Writing By JIDDARH UMAR 🌟🌙🌙🌙🌙🌙🌙🌟 *🌙✨MOONLIGHT WRITER'S ASSOCIATION🌙✨* https://m.facebook.com/Moonlight-writers-association-109698351308376/ *'''We are the moonlight writers we shine all over the world.''🌍'* ✍️✍️ بِسم الله الرحمن الرحيم ~~~~~~~💞💞~~~~~~~ *Ban yarda wani ko wata su saka min littafi a shafin su ko su mai da min littafi Audio ba tare da izini na ba* *23* *Wannan littafin nawa mai suna a sama na mai da shi na kuɗi,tare da Yar Tsanar Zinare,wanda yake son guda ɗaya dari uku 300,guda biyu 500 dari biyar, Hauwa Umar,Zenith Bank,2284905309,sai shaidar biyi ta wannan number 08141644865* Tana fita ƙofar gida ta gan shi tsaye da wata mata wacce makociyar suce basu daɗe da dawowa unguwar ba, Kallon shi take tun daga sama har ƙasa,sannan ta kalli kanta, Riga da zani ne a jikin ta na atamfa duk da ya dan fara kodewa amma fes yake,yaya Amina ce ta bata, Sai hijabi iya gwiwa wanda yake ruwan madara, Ji tayi wani abu kololo ya tsaya mata a makoshi, Yanzun wannan mutumin ne zata aura a matsayin miji,bata so ta tuna hakan,domin hakan ba karamin sosa mata rai yake yi ba, Jin matar na mashi magana ne yasa ta maida hankalin ta wurin su, "Almajiri,ko zaka dunga min tallan Pure water ina baka abinci? Dan ita tsakanin ta da Allah ta dauka Almajiri ne,saboda yanayin shi,kai ko wasu Almajiran sun fishi kyau gani. Kallon matar yayi daga sama har katsa,yama rasa ne zai ce mata, Ganin yana ƙoƙarin juyawa ne yasa ta kuma cewa"kai Almajiri da kai nake magana " Ranshi ne ya ɓaci,domin ya riga yaga Sumayya dake tsaye,ta yaya matar nan zata disgashi a gaban budurwar shi, Cikin jin haushi ya kalle ta yace"ki lalli miliyoniya kamata kice na maki tallah,to ko mijinki bai yi matsayin da zai zama dan aiki na balle ke kice zaki saka ni tallan ruwa,Idiot"nuna mata Sumayya yayi wacce ke tsaye tana kallon su"kalli matar da zan aura ko kyau ta fiki da wayewa,shine har zaki raina ni"ya karasa faɗa yana isowa inda take tsaye tana ji kamar ta haɗiye zuciyar ta,dan har wani kwanbo yake yi,wato shi a dole yana taƙama, Matar ce ta zo gabansu ta tsaya itama,sai da ta ƙare ma kowannensu kallo sannan ta kwashe da dariya tana nuna Sumayya da hannun, "Sumayya ko,eh in banyi karya ba kece Sumayya,wacce nake jin labarin ta anan layin,mace mai kyau da ji da kai," Dariya tayi tana nuna ta ta nuna Jauro"a gaskiya banyi tsammanin haɗewarki har yakai kina tsayawa da irin wadannan kananun yaran ba,ashema abinda ake faɗi akanki karya ne,gaskiya kin yi asara idan har kika auri wannan abun an ci baya"ta faɗa tana dariya tare da barin wurin tana jinjina lamarin. A cikin su an rasa wanda zai ce ma matar ko uffan,yanda kasan waɗanda aka rufe ma baki har ta bar wurin, Juyo da kallon shi yayi kanta suka haɗa ido, Kauda kanta gefe tayi tana haɗiye wani abu mai ɗaci da ya tsaya mata a makoshi, Shima shiru yayi yana kallon kanshi tun daga kan takalmin shi har kayan shi, Shi kanshi sai yanzun yake tunanin tabbas bai kyauta mata ba daya zo a haka,gashi har an fara gulman ta a kanshi,ko yace cin fuska, "Kiyi haƙuri" Cikin mamaki ta juyo tana kallon shi,domin tabbatar da cewa shin da gaske daga bakin shi maganar ya fito, "Kiyi haƙuri bai kamata na zo wurinki a haka ba,gashi na ja maki raini" Ita dai bata ce mashi komai ba, Ajiyar zuciya ya sauke "ni ba ɗan karya bane,ni ɗan ƙauye ne,ban iya dressing irin na samarin zamani ba,ban maki Alkawarin ba zan ƙara zuwa wurin ki a haka ba,amma dai zan kiyaye," Shiru yayi na wasu daƙiƙai yana kallonta yanda ta kauda kai, "Ki sani idan ina da ra'ayin canja tsarin rayuwata ya koma irin na ƴan karya ina iya canjawa a cikin Awa Ishirin da huɗu,sai dai ki sani ni ba zan yi haka ba,dan banda ra'ayin yin haka,saboda ke kuma ba zan canja ba,duk da ina sonki,na kuma yi Alƙawarin idan har na aure ki zan kula dake sosai,zaki samu jin daɗin da duk wani abu da kike mafarkin samu, Ni ban damu ba idan har baki sona,na maki alkawarin da zaran kin haifarmin yara guda biyu ko uku zan sallameki ki je ki auri wanda kike,ni kuma na kula da yara na,i promise you,kinga da anyi aure sai kiyi sauri ki zazzago min Ya'yana ni kuma na sallame ki,a yanda na yi lissafi acikin shekara huɗu idan Allah ya bani sa'a muna iya samun yara uku,shi yasa nake son ki kwantar da hankalin ki" Wannan karon daga kallon mamaki ta koma mashi kallon tsoro "anya kuwa wannan bai da matsalar kwakwalwa,in ba haka ba shi harya tsara mata yanda zata haihu,kuma tsabar rashin hankali wato har yana faɗa mata cewar zai rabu da ita da zaran ta haihu,to ita mahaukaciya ce da zata yarda ta haihu dashi" "Ba kada hankali" Tana faɗin haka ta juya ta shige cikin gida,idonta na kawo hawaye,waiyo ita kan Allah ya jarabceta,yanzun dama Jauro banda matsalar ƙauyanci da kazanta,harda matsalar hauka gare shi,kai Allah ya tsine ma Maman Momy. MaMa ce tace"waye ne awajen,naga kuma kin daɗe har ina shirin lekawa" "Jauro ne Mama amma ya wuce ko" "Me ya kawo shi kuma? " Mama nima ban sani ba,dan ban gane me yake faɗa ba" Shuru kawai Mamar ta yi dan ta lura kamar bata son yin magana kuma ranta a ɓace yake, Cire hijabinta tayi ta mika ma Aisha ta ajiye mata a daki sannan ta koma kicin tana duba wutar icen data hura,"in Allah ya yarda koda na aure ka babu wani abu da zan yarda ya shiga tsakani na dakai balle in haihu har ka mai dani bazawara,sai dai mu tabbata a haka "wannan shine abinda take rayawa a ranta. Jin sallamar Baba da tayi ne yasa taji gabanta ya faɗi,shi yasa bata juya ba taci gaba da aikin dake gabanta, Mama kuwa a inda take ma Aisha kitso ko kallon shi bata yi ba, Zuwa yayi ya ajiye babban ledan dake hannun shi a gefen ta,ya ja kujera ya zauna Ba tare data kalle shi ba tace"barka da zuwa" "Yauwa ya gida? " Lafiya " Bai damu da yanayin ta ba ya jawo ledan gabanta,"kiramin Sumayya " Kallon kofar kicin tayi"Sumayya," Amsawa tayi tana fitowa, Tana zuwa a gabansu ta tsungunna "Baba ina wuni" "Lafiya qlau yar Albarka,Sumayya Allah ya Albarkaci rayuwar ki,kuma maganar dana fada jiya na yafe maki harga Allah," Turo mata ledar gaban shi yayi"kinga dauki wannan ledar ki kaima mamarki daki ta raba ma ƴan uwa ta,domin goron saka ranar auren ki ne" Daga ita har Mama dago kai suka yi suna kallon shi cikin mamaki. Cikin masifa Mama take ƙoƙarin faɗin magana, Da sauri ta tari numfashinta"to Baba Allah ya kaimu" Daga shi har Mama kallon mamaki suke mata da jin abinda ya fito bakinta, Ta gefe ɗaya kuwa Baba cizan lebe yake yi domin yaso Mama tayi wata magana da babu abinda zai hana bai sake ta ba,kamar yanda Mama Mumy ta faɗa mai,da zaran ta mai maganar banza ya sallame ta ya huta kawai, Sai gashi ƴarta ta cece ta, Ƙoƙarin magana take ta kuma katse ta"Mama babu komai fa,karki manta mun riga munyi magana,so is ok"ta faɗa tana jinjina mata kai alamun tabbatar wa. Tare da daukar ledar ta shige daki, Cikin jin haushi ya ce"maganar me kuka yi? Cikin kauda zancen nashi tace"wani wata ne aka saka saka auren? Kauda kai yayi kamar bazai yi magana ba yace"nanda sati biyu,sannan in kin kaima ƴan uwanki Goro ki nima taimako a wurin su,domin ni ko kudin gado ba nida shi,nama godema Maman Momy tace zata ara min dubu hamsin sai a siyo mata gado wurin Dillaliya na hannu tare da katifa,idan yaso in an kawo sadaki sai a bata kuɗin ta, Sannan dama ina son in faɗa maki kardai kije ki gaiyata waɗannan ƴan uwan naki masu yawa,dan ko sunzo banda kudin da zan siyo abincin da za'a ci,sauran kayan daga baya idan anyi aure a hankali nata siya ana kai mata"yana gama fadar haka ya tashi ya fita ba tare daya bari ma ta samu dawowa daga shock ɗin data shiga ba. *idan kece Uwar Sumayya wani mataki zaki ɗauka* *🍂JAURO🍂* (MAI ANGUWA) Story & Writing By JIDDARH UMAR 🌟🌙🌙🌙🌙🌙🌙🌟 *🌙✨MOONLIGHT WRITER'S ASSOCIATION🌙✨* https://m.facebook.com/Moonlight-writers-association-109698351308376/ *'''We are the moonlight writers we shine all over the world.''🌍'* ✍️✍️ بِسم الله الرحمن الرحيم ~~~~~~~💞💞~~~~~~~ *Ban yarda wani ko wata su saka min littafi a shafin su ko su mai da min littafi Audio ba tare da izini na ba* *24* *Wannan littafin nawa mai suna a sama na mai da shi na kuɗi,tare da Yar Tsanar Zinare,wanda yake son guda ɗaya dari uku 300,guda biyu 500 dari biyar, Hauwa Umar,Zenith Bank,2284905309,sai shaidar biyi ta wannan number 08141644865* Tana daki tana jin duk abinda suke faɗa,rufe bakin ta tayi da tafin hannun ta tana ta faman kuka,wannan wani irin rayuwa ne haka,tunda Maman Momy ta shigo rayuwar su shikenan komai ya sauya masu,ba zata manta ba,haka lokacin auren Aunty Amina ya faru,ba karamin wahala tasha ba,dan ita a nata lokacin tana da saurayin da take so,amma maman Momy ta kawo mata wannan mutumin wai sai dai shi zata aura,gashi da mata har biyu ita ce ma ta uku,data ki yarda Baba har daure ta yake a ƙarfen Dish ta kwana a wurin, Duk wahala baisa ta amince ba sai da shi saurayin ganin wahalar da take sha yayi yawa ne yasa yace ya haƙuri kawai ta aure wanda iyayenta suka zaba mata,a ranar sai da ta kwanta asibiti tasha karin ruwa yakai leda takwas,yayin da shi kuma karshe ya bar garin, Daga karshe dai ba dan taso ba haka ta hakura ta aure shi, Indai wurin ciyarwa ne mutumin yana da ƙoƙari,haka tufafi dan gaskiya ba laifi,sai dai kuma yana da zuciya abu kaɗan duka,shi yasa har zuwa yau Aunty Amina bata kaunar shi,duk da sunada yara biyu,gani yake kamar siyan ta yayi,ba tada inci,haka in maganar zuwa gida ne gasu a gari daya jaha daya amma sai tayi wata biyar, shida bai bari ta leka gida ba, dan ba karamin kudin shi Maman Momy da Baba suka ci ba,kuma har yanzun a haka take kullun da kalan shaidar dukan da zaka ganta dashi a jiki ko a fuska, Wannan lamarin na damun Mama sosai,sai dai babu yanda ta iya tunda anfi ƙarfinta,Maman Momy kamar ta asirce kowa ba mai ganin laifin ta,da tayi magana sai ace zata kashe ma yarinya aure,shi yasa ta hakura kawai take binta da addu'a, Yanzun gashi abin ya zo kanta,sam bata son ta saka ma maman su damuwa dan idan abin ya mata yawa hawan jini na iya kamata,kwanaki ba jimawa da Aunty Amina tayi yaji mijin ya mata ɗan banzan duka,shine ta gudo gida, Shi kuma ya kira Baba ya faɗa mashi karya da gaskiya,ba tare da Baba yayi bincike ba ya hau kan maganar mutumin nan ya zauna, Har gida yazo ya same ta da cin mutuncin akan maza ta shirya tabi mijinta ta koma,ita kuma tace ko zai kashe ta ba zata koma ba,yayi bala'i har ya gaji ya wuce ba wanda ya kula shi, Da ya tashi sai zagaye ƴan uwan mama tare da nashi yayi yana fadin ai mama ta zugo Amina akan ta kashe aurenta ta hanata zaman gidan miji,haka yasa a wannan lokacin ƴan uwa suka juya mata baya,daga nata har na miji,babu inda take jin daɗi, Shi yasa akan Amina ta fauwala ma Allah komai. Zama tayi kusa da ita"Kuka kike yi Sumayya? Share hawayen ta tayi"A'a" Rungume ta tayi a jikin ta,nasan kin amince ne saboda kina gudun tozarcin da zai biyo baya daga gare ni,duk da kasancewar ki yarinya mai taurin kai,amma kina da tausayi na,kin damu da damuwa ta,ban so auren ki ya kasance haka ba,bana son rayuwarki ya kasance tamkar irin nawa dana ƴar uwar ki,naso koda ke din ce ki samu kwanciyar hankali,amma babu yanda na iya,kin gama min komai,ina maki fatan nasara a rayuwar ki,kamar yanda kike da ƙudurin taimaka min a rayuwar ki,Ubangiji ya taimaka maki,kar ya taɓa barin ki tabewa,Allah ya zama gatanki,kamar yanda kika so ki zama gatan mu, Na san idan ace a yau ina da iyayen da zasu tsaya min ne da hakan ba zai faru dani ba balle ku,sai dai na taso ne ni ma a gidan da ba'asan daraja taba, Nasan ba ni da abinda zan iya baki daga yanzun har a kaiki dakin mijin ki,haka kuma ba zan taba roƙon ƴan uwa na ba domin su taikama min,sai dai ina iya baki dama akan kiyi kuka a kafaɗa ta iya yanda kike jin zuciyar ki zata yi sanyi,"ta fada tana ƙara rungume ta, Kuka ta fashe dashi tana kara rungume Mama,yayin da ita kuma take shafa bayanta a hankali. ___________*Gidan Maman Momy* Baka jin tashin komai a tsakar gidan sai tashin dariya, Zaune suke sun baje a tsakar dakin ko wacce da kwalbar kok a gabanta,su uku ne. Daya daga cikin su ne ta sheke da dariya "shegiya Asma'u ba kida dama,wato dai ba zaki mata da sauƙi ba" Maman Momy ce naga ta kai ma matar data yi magana duka a cinya"waya faɗa maki ana sanya a zamanin nan Blessing,ai idan kace zaka zauna sai kaga ta zama,shi yasa kika ga tunda na shigo gidan nan a tsaye nake na hanata rawar gaban hantsi,bata isa ta motsa ba,ya'yanta ma ba tada ikon da zata aurad dasu sai mijin dana zaɓar masu,dan nasan idan suka aure masu kuɗi ko gidan hutu to Uwar su ta huta,ni kuma abinda ban so kenan " "Amma fa Asma'u zance ko Julia ba kiɗa mutunci,kamar ba tare kuka tashi da Maman Sumayya ba,yanzun da kike mata haka wa zai ce kawarki ce,ita ta musuluntar dake,ta baki kaya,kar ki manta kawarki ce sosai a wancan lokacin,amma kika mata cin amana kika aure mata miji kika hanata kwanciyar hankali,lallai kin cika butulu,na jinjinama makircin ki,dole na zo daukar darasi na musamman " Hararanta tayi"bana son iskanci Abigil,ni har mantawa nake na ta fitowa daga jinsin kiristen,batun wancan matar kuma tamin komai ai bai taso ba tun da ban taba rukonta ba" Ihu Blessing ta saka"Jesus,Julia kar ki manta nan har rokon Maman Sumayya pant kike da Bireziya,batun rokon abinci kuwa ba'a magana, shine yanzun tsabar samun wuri zaki faɗi haka,Jesus karya babu wuya yanzun" Tsaki taja tana murguda baki"ay koma dai menene a da ne,yanzun kuma fa,ai dai nafi ƙarfinta,kuma sai yanda nayi da ita da ya'yanta har ma da mijinta," Duk kallon juna suka yi suna tabe baki,dama haka ɗan adam yake bai iya samun wuri ba,domin duk a unguwa daya suka tashi dukkan su,wanda ya ke haɗe da Arna da Musulmai,kuma a wannan lokacin suna zaman lafiya sosai, Amma shine taci amanar kawar ta,koma dai yaya ne su babu ruwansu tunda dai in sun zo ana ɗan siya masu kok... *🍂JAURO🍂* (MAI ANGUWA) Story & Writing By JIDDARH UMAR 🌟🌙🌙🌙🌙🌙🌙🌟 *🌙✨MOONLIGHT WRITER'S ASSOCIATION🌙✨* https://m.facebook.com/Moonlight-writers-association-109698351308376/ *'''We are the moonlight writers we shine all over the world.''🌍'* ✍️✍️ بِسم الله الرحمن الرحيم ~~~~~~~💞💞~~~~~~~ *Ban yarda wani ko wata su saka min littafi a shafin su ko su mai da min littafi Audio ba tare da izini na ba* *25* *Wannan littafin nawa mai suna a sama na mai da shi na kuɗi,tare da Yar Tsanar Zinare,wanda yake son guda ɗaya dari uku 300,guda biyu 500 dari biyar, Hauwa Umar,Zenith Bank,2284905309,sai shaidar biyi ta wannan number 08141644865* Kiran Baffa Bube ne ya ta da shi barcin da ya koma bayan sallar Asuba,dan ranar bashi aiki yana hutu, Faɗa mashi yayi akan yana nimanshi a gida yanzun, Dole ya tashi ya kintsa sannan ya dauki hanya, Kwata_kwata tafiyar awa daya ne ya kaishi ƙauye, Koda ya isa a ƙofar gidansu ya same su zazzaune harda yaran Baffa Sanda,su Yabbale, Sallamah ya masu sannan ya samu wuri ya zauna,bayan ya ƙara jajanta masu abinda ya faru, Baffa Bube yace Audu dan gidan Goggo Badejo ya je cikin gida ya kira Dan Fodio,tun dazu zaman jiranshi suke yi da tuni sun fara,amma ya tsaya yana ja masu rai kamar wasu ƙananun yara. Yana fitowa zama yayi ba tare daya ce ma kowa komai ba, Suma kuma basu kula shiba, Baffa Bube ne ya fara magana "kai tsaye na tara ku ne domin na sanar daku mutanen da suka dauke Sanda sun kira,sun kira mun yi magana dasu sunce suna buƙatar Miliyan goma ko wanni mutum daya,wato dai shida kande,wanda kuɗi ya tashi miliyan Ishirin, Na dai roƙe su akan su rage mana akan mu bada miliyan goma,basu yarda ba wai sai dai a basu sha-biyar ko kuma su kashe su, To ku me kuka gani? Gabaɗayan su shiru su kayi,kowa na jinjina yawan kuɗin, "Ba shiru ya kamata ku yi ba,kamata yayi a san abun yi" "Abun yi ɗaya ne,shine kawai ƴa'ƴan shi su fitar da kudi su amsoshi,in basu dashi su fitar da dabbobinsu a sai da" "Wannan wani irin maganar banza ne haka kake faɗa Ɗan Fodiyo" Cewar Audu. "Ai ba maganar banza na faɗa ba,idan ku kunada kudun da zaku bada to ni dai banida shi," "Kai wai m... " Ya isa haka Audu,kyale shi,mu da yake uban mu ai dole duk yanda zamu yi muyi domin mu amsoshi,"cewar Yabbale "Ban taraku dan kumin rashin hankali ba,dan haka ko wannen ku ya saurare abinda zan yanke mashi wanda zai bayar" "Dukkan ku manya zaku bada budu dari biyar_biyar, ko wannen ku,bana son jayayya" Mikewa tsaye yayi"haba Baffa,wani irin dubu dari biyar,ina na ganshi,ita kake son mu samu,ni dai gaskiya banida halin shi" "Dottiya ne ya ce Baffa gaskiya sai dai ya'yan shi su sai da dabbobin su a biya,dan ni dai Bani da shi," "Ai dama ba nimam taimakonku muke yi ba,ko da zamu sai da rabin dabbobinmu mu zamu amso mahaifin mu" Yabbale ya faɗa cikin jin zafin abinda suke faɗi. "Ya isa haka duk ku zauna" Baffa ya faɗa Sai dai ko kallon shi babu wanda yayi,sai ma wucewa dasu Yabbale sukayi, Kallon Jauro yayi wanda tunda aka fara magana bai ce komai ba,sai dai ya kalli wannan ya kalli wancan "kai ba kada abinda zaka ce ne? " Eh ina da abin faɗa Baffa " Maida hankalin shi yayi kanshi daga kallon su Ɗan Fodio da suka wuce suna faɗa,"ina jinka" "Baffa yarinyar da zan aura iyayenta sun ce na turo magabatana,kuma nan da sati biyu suke son ayi bikin,to ni kuma gaskiya bansan yanda zan yi ba saboda ga batun kama su Baffa da batun amsosu da ake yi,sai dai wallahi Baffa bana son na rasa yarinyar dan ina son ta" Ɗan karamin tsaki ya ja"ni ba wannan maganar nake ji daga bakinka ba,maganar kuɗin da muka yi yanzun nake son naji yaushe taka ba da naka,idan har ka bada naka bani da damuwa a kan batun auren ka,kaga ko Malam liman yana iya zuwa yayi komai " "Baffa bada waɗannan kudin abu mai sauƙi ne,dan haka a dauki shanaye na dake wurinka guda uku a sai da shi sai a bada nawa kuɗin" Abin mamaki nan take sai ga fuskar Baffa Bube ya hade kamar hadarin gabas,cikin bacin rai yace"wannan wani irin maganar banza ne haka kake faɗa Jauro,to in dai Shanayen ka na wurina ka saka ma ido to sun kare tun tuni " "Sun fa kare,ni da ko daya ban taba amsa ba a wurunku,ba mutuwa su kayi ba sannan yanzun ace sun kare? Cikin inda_inda yace" To me kake son in ce maka,lokacin kana makaranta wannan mutumin yazo wai kana buƙatar kuɗi,to shine na keta saidawa ina bashi kudin yana tura maka" "To na wurin Baffa Sanda fa? " Kai ina ga da wuya in za'a samu abin da ya rage a hannun shi," "Yanzun kenan ni dai ne a gidan nan ba ni da ko ƴar kaza,? Ya faɗa yana jin zafin abin a zuciyar shi,duk da dama ya riga ya saka a ranshi ba samu zai yi ba,amma kuma jin haka daga gare su ya fi mashi zafi,idan yayi duba da ko yaro ƙarami in dai a gidan aka haifeshi to yana da abin kiyo, Girgiza kai kawai yayi " In dai haka ne Baffa sai dai ince Allah ya kyauta,dan ba ni da ko dubu hamsin din da zan bada balle dubu dari biyar," "To shi kuma auren da kace zaka yi fa,da wani kuɗi zaka yi su? Baffa ya tambaya cikin yanayi na rashin damuwa,dama fargabanshi daya kar Jauro ya tada rigima akan bai yarda ba sai sun fito mai da dabbobin shi, To ya gode Allah tunda yaron bai dau abin da zafi ba, "Dama akan dabbobina na saka rai,amma tunda abun ya kasance haka,kuma ina son yarinyar,zan roki mahaifinta akan ya Bani bashin aurenta in yaso daga baya na bata kuɗin Sadakinta" "Yanzun kai Auren bashi zaka yi,wai duk ina kuɗin aikin kwamnatin da kace kana yi a cikin gari? " Baffa ko zaka aramin ne? Tsaki yaja ya tashi "kaje dai ka sami Malam Liman na tabbatar idan yana da shi zai baka"ya faɗa yana barin wurin. Girgiza kai kawai yayi ya nufi gidan Malam Liman domin sanar dashi yanda suka yi da Baffa Bube...... *🍂JAURO🍂* (MAI ANGUWA) Story & Writing By JIDDARH UMAR 🌟🌙🌙🌙🌙🌙🌙🌟 *🌙✨MOONLIGHT WRITER'S ASSOCIATION🌙✨* https://m.facebook.com/Moonlight-writers-association-109698351308376/ *'''We are the moonlight writers we shine all over the world.''🌍'* ✍️✍️ بِسم الله الرحمن الرحيم ~~~~~~~💞💞~~~~~~~ *Ban yarda wani ko wata su saka min littafi a shafin su ko su mai da min littafi Audio ba tare da izini na ba* *26* *Wannan littafin nawa mai suna a sama na mai da shi na kuɗi,tare da Yar Tsanar Zinare,wanda yake son guda ɗaya dari uku 300,guda biyu 500 dari biyar, Hauwa Umar,Zenith Bank,2284905309,sai shaidar biyi ta wannan number 08141644865* Duk da cewar lokaci ya ja bakaman da ba,amma Malam liman bai bar zama yana koyar da ɗaliban shi ba, Dan haka samun wuri yayi ya zauna a cikin Almajirai har aka idar karatu suka yi Addu'a suka watse, Sake sabon gaisuwa suka yi da Liman,inda yake faɗa mashi yanda suka yi da Baffa Bube, "Hakan da kayi shine daidai Jauro,domin shi Gado ba abin fitina ba ne,yau ina asalin wadanda suka tare dukiyar suke?sun tafi sun bar ta ba dan suna so ba,to kamar yanda suka tafi suka bar ta muma haka zamu tafi mu barka,ko kuma ita ta tafi ta bar mu,na gode ma Allah da baka tada hankalin ka ba akan haka,Allah kuma ya ƙara hore maka naka," "Amin Malam" "Batun niman Auren ka kuma,In Allah ya yarda jibi Laraba zamu je akai kudin sadakin," "Amma Malam kana ganin babu matsala idan akayi komai bayan ba'a sake Baffa Sanda ba,ba zasu kullace ni ba" "Ina ce a gabanka ya faɗa kayi auren ka kawai,kuma in dai ba kayi karya ba ai inaga ba matsala,ko za ku wani wasa ne? Da sauri ya girgiza kai" A'a dan yanzun ba ni da wasu kuɗi a kasa saboda na kashe kuɗi sosai wurin turo takardu na UK," "To ba damuwa,hakan yayi Allah ya taimaka" "Amin" Ya fada ya na yi mashi sallahma. _______kamar yanda Malam liman ya tsara haka kuwa aka yi,domin an kawo sadakin Sumayya wanda Baba ya karba dubu dari,sai dukiyar aure kuma suka bada dubu dari uku, Ranar Baba bakin shi har kunne,domin bai ɗauka zai samu koda rabin haka ba,dan su sun bashi dukiyar aure ne bisa Al'adun su na Fulani, An kuma saka biki nan da sati ɗaya,wanda ya kama ranar Juma'a. Kamar yanda bai ba Sumayya ko sisi ba haka ita ma Mama bata ga kudin ba,illa dai faɗa mata da yayi ga kudin da suka bada,amma ya ba maman Momy ta siyo mata wasu yan kayayyaki na mata na buƙata,dan tace a kwai in da zata siyo komai cikin sauki,a rahusa mai kyau. Ita dai Mama har ya gama magana ba tace masa ci kanka ba,har ya kammala fada ya juya zai tafi,sai kuma ya juyo ya kalle ta ganin yanda tayi ko in kula da shi"to ke baza kice komai ba ne? "Allah ya sanya Alkhairi" Waro ido yayi"kawai," Cigaba da ninke kayan Aisha da aka wanke tayi, "Abinda kawai zaki ce kenan," Murmushi mai sanyi ta sakar mai,"me kake son in ce bayan addu'ar da nayi,so kake kaga ina tashin hankali ina hauka,shin koda nayi hakan zai sa ka fasa yin abinda kayi niya ne?A'a fa,dan haka ni na barma Allah komai,duk abinda yayi a kansu daidai ne,na tabbatar da ba zai bari nataɓa jin kunya in sha Allahu tunda nayi imani dashi,kuma ya'ya na ba zasu taɓa wulakanta ba,in dai Aure ne a je ayi,ko gobe kaga dama a dauro ma Sumayya aure,Allah ya basu zaman lafiya"tana gama faɗar haka ta tashi ta bar mai dakin, Jikin shi ne yayi sanyi domin bai taɓa tsammanin haka daga gare ta ba,a tunanin shi idan ya faɗa mata zata kusa haukace mashi,sai gashi ta bashi mamaki, Shi kanshi wani lokaci idan ya kalli fuskarta ya kanji a ranshi bai mata adalci ba ita da ya'yanta,a duk lokacin da yayi niyar kure ta,sai ya ga abin mamaki,domin sai ta nuna mai babu komai,koda kuwa ita aka cuta,sai tayi haƙuri, Ya mata abubuwa da yawa wanda ya kamata ace ta bar shi,sai dai har yau wani abin yana mashi nauyi a zuciya,yana ganin kamar har tana kallon shi dashi taki mashi magana ko ta tuhume shi akan hakan,shi yasa wasu lokutan yake jin haushin ta dan a ganin shi ƙeta ne take mai,ta bar shi na nauyin zuciya,domin tun daga lokacin da ya aure kawarta Aminiyar ta nar suka zauna zaman wata bakwai ba tare data san ƙawarta ce ya aura ba,duk da dama ba gida ɗaya suke ba,sai bayan wata bakwai ne take samun labara abakin iyayen ita Maman momy wanda suma basu san bata sani bas Har izuwa rana ta yau bata taba buɗe baki ta tuhume shi akan haka ba, Son zuciyar shi ne ya jawo komai,sai dai gaskiya ba yajin zai iya mata adalci,yasan zata ci gaba da hukuri dashi har zuwa ƙarshe tunda tana son shi(har kaban tausayi Baba) tashi yayi ya karkade rigar shi ya bar gidan. Kuka tayi sosai a cikin dakin da ta shiga,ji take kamar numfashin ta zai ɗauke saboda yanda ta ji wani abu yazo ya mata tsaye a dai-dai saitin zuciyar ta,baƙin ciki take ji da kunci mai daɗi,ta rasa wanda zata faɗa ma damuwarta ta ji sauƙi,ya'yan ta ne kawai take dasu,ba zata iya faɗa masu ba,saboda ta san ko wannen su na fama da tashi damuwar wanda ba zataso ta ƙara masu da nata ba,sai dai ta san komai lokaci,ita dai fatanta daya ne,shine Allah yaji tausayin ta ya rangwanta mata,ko da takan Sumayya ne,yasa ta samu kwanciyar hankali,domin samun kwanciyar hankalin daya daga cikin su tamkar rage wani bari ne daga cikin damuwarsu. ________zaune take ta rabka uban tagumi tayi zurfi cikin tunani,gabaɗaya ta rasa ne ke mata daɗi a duniya,ji take tamkar duk wani jin daɗi na rayuwar ta ya yanke,duniyar ma juya mata yake, Jin an sauke mata hannu ne yasa ta sauke ajiyar zuciya ne nauyi, "Haba mana Sumayya,so kike ki hallaka kanki da tunani,karki manta da komai yayi zafi maganin shi Allah,pls ki rage wannan tunanin da kike yi" Kara sauke wani ajiyar zuciyar tayi wanda a yanzun ya biye mata jiki,"Salma ba za ki gane bane,amma duk yanda naso na cire abin a zuciya ta na kasa,ba wai auren nan ne bana so ba Salma,ba kuma batun shi ne kaɗai ke damuna da kuma tayarmin da hankali ba face lamarin Baba da Mama,kullum lamarin Baba ƙara yin gaba yake,to ya zan yi,ɗan sana'ar da Mama ke yi sama_sama duk jarin ya kusa karewa,ƴan uwanta har yanzun ba wanda yace komai game da wannan auren,ita kuma ba wai tana da shi bane,ni dai nasan kawai sai yanda Allah yayi da rayuwata"...... Kuyi haƙuri da wannan,in sha Allah zan kara yawan page *🍂JAURO🍂* (MAI ANGUWA) Story & Writing By JIDDARH UMAR 🌟🌙🌙🌙🌙🌙🌙🌟 *🌙✨MOONLIGHT WRITER'S ASSOCIATION🌙✨* https://m.facebook.com/Moonlight-writers-association-109698351308376/ *'''We are the moonlight writers we shine all over the world.''🌍'* ✍️✍️ بِسم الله الرحمن الرحيم ~~~~~~~💞💞~~~~~~~ *Ban yarda wani ko wata su saka min littafi a shafin su ko su mai da min littafi Audio ba tare da izini na ba* *27* *Wannan littafin nawa mai suna a sama na mai da shi na kuɗi,tare da Yar Tsanar Zinare,wanda yake son guda ɗaya dari uku 300,guda biyu 500 dari biyar, Hauwa Umar,Zenith Bank,2284905309,sai shaidar biyi ta wannan number 08141644865* "In dai haka ne kam dole ki damu,ba ma ɗan kaɗan ba,amma ki sani damuwa baya maganin komai sai dai ma ya illatar dake,wanda hakan zai ƙara ma Mama damuwa da tashin hankali ne,dan haka Addu'a ne kawai mafita" "Allah ka fitar dani"ta fada tana mikewa" Salma yaushe zaki shigo? "Zan shigo amma sai zuwa jibi,dan gobe zamu fita da Inna,amma fa ki faɗa ma Jauro ya ajiye mana kuɗin ƙawaye" Tsaki taja"in dai wannan ɗan iskan ne dai-dai yake daku ai " "To ki bani numbar shi,dan wallahi dole mu kwanci wani abu a hannun shi duk makon shi, kuma sai ya mana wasa dan party zamu haɗa" Tafiya ta fara"ai na faɗa maki ba ni da number shi,kuma in dai wannan ne zaki ce na faɗa maki,"ta faɗa suna fita tare. Washegari sai gani suka yi ana shigowa da kaya niki_niki,ita a lokacin ma ta fito wanka ne tana so taje gidan Aunty Amina wacce tunda aka fara maganar bikin mijinta bai bari ta zo ba, Daya daga cikin yaran Mama ta tsayar "kai waɗannan kayan kuma daga ina" "Baban Aisha ne yace mu shigo dashi" Shiru tayi tana kallon su har suka kammala shigowa da duka kayan,sannan ya shigo da dariya a fuskar shi, "Yauwa ashe kuna tsakar gida" Nuna mata kayan ya yi"kinga ga kayan dakin Sumayya,sunyi kyau sosai ko,ai Maman Momy ba karamin ƙoƙari tayi ba har sai da ta cika dubu goma,zuwa yamma Sumayya ta shirya ta je ta mata godiya" Ita Mama ta ma kasa magana sai kallon kayan da take yi, Cikin tsananin takaici da ɓacin rai tace"Baba yanzun waɗannan kayan sune kayan daki na,sai kace na wata tsohuwar bazawara,kalli fa katifar duk jurwayen fitsarin yara,zanin gadon yayi baki kirin da dauɗa duk ya yayyage,Tukwane duk baki kirin alamun sunji jiki,duk cikin kayan nan babu na ar...." Kuka ta fashe dashi wanda bata san sanda ya fito ba,ta juya da gudu tana shigewa daki, Kallon Mama yayi baki buɗe "Amma yarinyar nan ba tada godiyar Allah,ki duba kiga duk irin kokarin da matar nan tayi amma abinda zata ce kenan,kalli wancen kulan me kyau dashi,to wallahi ki ja mata kunne,kin ga dai aure zata yi,in ba haka ba zan faɗa ma mijinta ya ringa mata dukan tsaya ko zata yi hankali, k.... Ita ma juyawa tayi ta shige ɗakinta ta bar shi nan a tsaye, " Kai ni bansan me naye ma Allah ba daya jarabce ni da irin wannan matar da Ƴar,dole na koma Istigfari"ya ja tsaki yana barin gidan. Ta kasa kuka ta kasa yin komai,kawai dai tayi shiru ne ta zauna wuri ɗaya ba tare da ta san tunanin me take yi ba, Can kuma kamar wacce ta tuna wani abu,da sauri ta mike ta nufe dakin Sumayya, Kwance take a bakin gado tana ta faman rusar kuka,a jiyar zuciya ta sake tana zama kusa da ita tare da jawo ta jikin ta"in sha Allahu wata rana sai labari,ki dai na kuka domin ba zai canja komai ba sai abinda Allah yayi," Cikin tsananin kuka wanda muryarta ma da kyar take fita"Mama me yasa Baba baya son mu ne,ko dai bashi bane ya haife mu? "Subhanallah me kike faɗa ne haka Sumayya! Ba kuda wani Mahaifi da ya wuce shi,shine ya haife ku,kuma duk abinda kika ga yana yi bawai yana yi bane dan baya son ku" Taran numfashin ta tayi"to don me yake yi? Me yasa baya ma su Momy?Baba yasan buri na tun ina kara na girma nayi karatu ta yanda zan iya taimaka maki,amma tun ina aji uku ya bar biya min kudin makaranta,ke kike biya min kudin har izuwa lokacin dana kammala NCE,a lokacin da nake ganin na kai matsayin da zan taimaka maki,a wannan lokacin shi da matar shi suka durkushe ni,suka tarwatsa burikana, Ban taɓa sanin dalilin da yasa tun ina karama bana son Baba ba sai yau,saboda komai baya mana shi cikin adalci,"dago kai tayi daga jikinta suna fuskantar juna "Mama me yasa baki bar Baba ba kin gudu?me yasa baki koma gidan yan uwanki ba,Baba baya son mu,ɗan Allah mu gudu,ni na gaji ba zan iya ba" Ji tayi wani irin hawaye me azaban raɗaɗi kamar Barkono ya zubo daga cikin idonta,wanda sai da ta lumshe idon na ɗan wani lokaci kafin ta dube sunyi jawur wanda shi zai tabbatar maka da irin azabtuwa da zuciyar ta keyi,da kyar ta iya buɗe bakinta wanda taji yayi mata ɗaci da nauyi "saboda mahaifinku shine rufin asiri na! Idan na bar gidan nan daku ina zanje?gidan waye zan je ya karɓe mu ni da ku?Sumayya kina ganin yanda ƴan uwa na suke,kowa na fama da kanshi,ba ni da wurin gudu,ni kai na nasan yana zaune da ni ne dan na zame masa tamkar dole,in da ace iyaye na nanan ne da hakan be faru ba,kiyi haƙuri Sumayya! Kiyi haƙuri,ba ni da yanda zan yi!ki taya ni karɓar wannan ƙaddaran dan Allah mu ci ta tare,kome kika gani kije kiyi haƙuri dashi dan Allah yata "ta faɗa tana haɗa hannayen ta wuri guda alamun roƙo. Da sauri ta daura hannun nata saman na mahaifiyar nata," Mama!dan Allah ki dai na roƙo na,in dai ina raye sai kin bar irin wannan rayuwar,sai na zama abinda zaki yi alfahari,wata rana sai kin zauna a gidan ki na kan ki,in da babu wanda ya isa kiji tsoron shi ko kiyi tunanin wani zai iya koran ki,in da zai zame maki mafaka in Allah ya yarda" Rungumi ta tayi tana saka mata Albarka, Yinin ranar sun yi shine cikin rashin walwala da daɗin zuciya, Sai da ya rage saura kwana uku biki sannan ƴan uwan Mama suka fara tuntuɓar ta akan ya maganar biki,shima sai da kanin Baban su ya saka baki shi ne fa suka zo,shima basu wani jima ba suka tafi dan ba wani aiki ko wani shagali da za'a yi,dan yace duk abinda zata yi sai dai ta tattara mutane ta su je gidan maman Momy dan ya bata komai na girki a can za'a yi taro, Dasu Yaya Babba da Aunty Rahima suka tambayeta ta fada masu yanda suka yi dashi,cewa suka yi sukan ba wanda ya isa ya kai su gidan maman Momy bayan ga gidan Uwar yarinya,dan haka ba zasu je ba"ita ma bata da ba goyon bayan akan su je ba,kuma bata ji haushin su akan haka ba, Washegari Alhamis wanda yayi dai-dai da gobe ɗaurin aure ne yan gidan Malam liman suka kawo kaya aƙwati dana saka lalli,sai da suka fara kaiwa gidan Maman Momy dan nan aka jwatanta masu kafin a saka ƙanin Momy ya masu jagora har kofar gidan ya juya, An tarbe su cikin mutunci aka kuma shinfida masu tabarma a tsakar gida in da mutane ke zaune,Akwati ne guda biyu na fata,sai tirmun zani uku masu kyau dana roba biyu,Les daya shadda daya, A ɗayan kuma ƴan kayan kwalliya ne da darduma sai Kur'ani,shi kenan, Ba wanda ya nuna masu komai dan da zasu tafi harda dubu daya Mana ta bada aka basu,wanda ba karamin daɗi suka ji ba, Bayan tafiyar su ne Aunty Rahima ta kalli kayan a wulakance ta sheke da dariya,"kai ke dai wallahi Wasila ba kida sa'a a rayuwa,ki duba yanda aka yi auren Amina,ko da yake har Gara na Amina akan Sumayya,ace duka ya'ya ba in da suka dace,wallahi ban iyawa da wannan kayan takaici " "Ke wallahi suma matsiyata ne,ko da yake ke baki ga zubinsu ba daga dukkan alamu daga kauye suke,ƙila ma mai kiyo ne,kai Allah ya shirya Baban Aisha ko ina kuma yaje ya rarumo wannan mutumin oho,Allah yasa shi ba mai duka bane kamar Mijin Amina" Haka dai sukai maganganu marasa daɗi a kan Mama da ya'yanta,sai dai ba tace masu komai ba,illa dai addu'ar da taita yi acikin zuciyar ta dan niman sassauci daga Ubangijin ta. A washegari da safe ƙarfe goma jama'a suka shaida ɗaurin auren JAURO da Amaryar sa Sumayya, kamar yanda Allah ya halasta, Yayin da Amarya take can kwance tana fama da a zaɓaɓɓen zazzabi dan har bata san wanda ke tsaye a kanta ba...... *To fa,yanzun Aka fara* *🍂JAURO🍂* (MAI ANGUWA) Story & Writing By JIDDARH UMAR 🌟🌙🌙🌙🌙🌙🌙🌟 *🌙✨MOONLIGHT WRITER'S ASSOCIATION🌙✨* https://m.facebook.com/Moonlight-writers-association-109698351308376/ *'''We are the moonlight writers we shine all over the world.''🌍'* ✍️✍️ بِسم الله الرحمن الرحيم ~~~~~~~💞💞~~~~~~~ *Ban yarda wani ko wata su saka min littafi a shafin su ko su mai da min littafi Audio ba tare da izini na ba* *28* *Wannan littafin nawa mai suna a sama na mai da shi na kuɗi,tare da Yar Tsanar Zinare,wanda yake son guda ɗaya dari uku 300,guda biyu 500 dari biyar, Hauwa Umar,Zenith Bank,2284905309,sai shaidar biyi ta wannan number 08141644865* Ƙarfe huɗu na yamma Baba ya shigo da kanshi yace maza masu kai amarya su zo su tafi dan baya son tafiyar Magrib, Aunty Rahima ce tace ma Mama tazo suyi sallamah da Sumayya, Cewa kawai tayi su tafi da ita Allah ya bata zaman lafiya, Tana kwance a ɗakin ta Salma da Aunty Amina suna tsaye a kanta,sun rasa yanda zasu yi da ita,domin gabaɗaya jikinta ba ƙarfi gashi yayi zafi sosai dan har kaduwar sanyi take yi, "Wai me haka kuke yi ne a tsaye Amina,tun dazu ana jira ku fito da yarinya amma kun tsaya" "Yaya Babba jikinta ne yayi zafi gashi tana rawar sanyi shi yasa" Tsaki taja tana yaye lullubin da tayi"Oya tashi mu tafi" Da kyar ta iya buɗe ido "yaya Babba ba zan iya tashi ba" "Ke tashi bana son lalaci" Ta faɗa tana jawota ta miƙar da ita,tare da yafa mata mayafi Babba,sai dai taku biyu kawai suka yi ta yanke jiki ta faɗi, Salati suka saka suna nufar kanta,amma ina domin tayi nisa,ruwa aka diba aka shiga yayyafa mata,amma shiru kake ji babu magana domin ko motsi bata yi ba, Hankalin mutane ya tashi,dan haka dole aka dauke ta aka yi asibiti da ita, Suna isa gado aka bata cikin gaggawa,kafin Aunty Babba ta kira wayar Baba, Sai da tayi kira uku sannan ya ɗauka,"wake magana? "Yaya Babba ce,so nake na sanar da kai muna Asibiti tare da Sumayya dan ta suma,kuma gashi har an bata gado,ka turo yaro da kudi Asibiti Mata ya kawo mana ko da dubu biyar ne" "Me?dubu biyar?to ni nan ko ɗari biyar bana magani ɓalle wani dubu biyar,kinga Yaya Babba ki kira uwarta ko mijinta su turo kuɗin,sannan idan ta farka kar ku dawo da ita gida,akwai motoci biyu da mijin ya turo na ɗaukar Amarya, zan turo maku shi yanzun su zo," Yana gama faɗar haka ya kashe yawa. Shiru kawai tayi riƙe da waya a hannun ta,wannan wani irin mutum ne shi haka mara imani,haba sai kace ba yar shi ba, Komawa tayi kusa da su Aunty Rahima ta zauna wacce ke tambayarta ya suka yi dashi,nan ta kwashe yanda suka yi ta faɗa mata,sai cewa tayi"ni da ban fito da kuɗi ba,sai dai in zamu kira Wasila ta turo kuɗin " "Ke ma dai kinsan fitowar dubu biyar daga Aljihunta ba abu me sauki bane,tunda ba wai tana da shi ba ne" "To kuɗin da muka haɗa mata fa,naga dai ba wani abun da aka siya da shi" "To abincin da kika ci fa,ai dashi akayo cefane a kayi girki" Tsaki taja tana turo baki"Allah ya rabumu haɗa jini da zuri'ar tsiya " Wata Nus ce suka ga ta taho wurin yayin da wasu Maza su uku ke biye da ita,"gasu nan "Nus din ta faɗa tana nuna su. Daya daga cikin su wanda yake haɗaɗɗe a cikin su,kai daka ganshi kaga kalan ƴan gayu,ya matso in da suke" Mama ina wunin ku" Cikin sakin fuska suka amsa,yayin da sauran ma suka gaida su,sai dai su din kam ba laifi,duk da ba kamar ɗayan ba a wurin wayewa. "Mama ni sunana Muntaz,abonki Jauro,sai wannan shi kuma Muhammad,da Abdullahi,dukkanin mu abokai ne,dama mun je gida ne daukar Amarya shine Baba ya sanar da mu abinda ya faru,Ya jikin nata? " Jiki da sauƙi,an samu ma ta farka,ta dan samu barci ne amma yanzun zan tada ita sai mu je"cewar Aunty Rahima. "No just live her,idan ta tashi sai mu dawo" "Ku dai ku jira mu a waje" Amsawa suka yi suna fita don su jira su ɗin, "Aunty ga dubu biyu dake hannu na sai a haɗa a bada kudin maganin"Amina ta faɗa. Harara Yaya Babba ta zuba mata" To a cikin mu wa kika ga ni da kudi,gara in ki nada sauran ma ki fito dashi mu tafi" "Wallahi Aunty ba ni da shi,iyakar kuɗin kenan" Kafin ta bata amsa ne Nus ta katse su tana ajeye masu Ledojin magani a gaban su"ga magungunan ta,an rubuta yanda zata sha kowannensu a ciki,Allah ya kara sauki"ta fada tana juyawa. Da sauri Aunty Rahima ta tsare ta"To ai ba mu biya kuɗin maganin ba naga kin kawo mana magani " "Ai waɗannan samar dazu sun biya kuɗin komai,dan haka kuna iya tafiya,sai dai ita mara lafiya ta yi ƙoƙari ta ci abinci kafin tasha magani" "To mun gude" "Kai Alhamdulillah komai yazo mana da sauƙi,Allah mun gode maka" Cewar Amina cikin farin ciki,dan dama har ta fara tunanin ta ina maman su zata fara. Ta da ita Aunty Babba tayi,ba dan taso ba haka ta tashi da taimakon Amina,dama kuma ba barci take yi ba tunda ta farka duk abinda suke yi tana jinsu, Suna fitowa a harabar Asibitin suka same su a tsaye jikin wasu lafiyayyun mota,Muntaz (ɗan Alhaji) shi ya nuna masu motar da zasu saka Amarya,suna ƙoƙarin shiga ne sai ga Salma ta shigo Asibitin wacce ta sauka saman abin hawa, Amina ce ta kwalla mata kira,dan haka tare da ita aka tafi, Kamar yanda Jauro ya masu kwatancen gida haka suka bi kwatancen har ƙofar gidan wanda da su Amina sun san gidan tunda jiya sun zo sun kawo kaya, Gidan ƙaramin Flat ne mai dauke da babban falo sai daki daya da bayi sai kuma tsakar gida da kicin a tsakar gidan, Ba laifi sun samu tarba daga yan gidan su Muha da Malam Liman, Abinci kuwa mai rai da lafiya aka basu wanda daga ganin shi kasan basu suka girka ba,yaji Manya-manyan kifaye da naman kaji,sunci sun ƙoshin dan su Yaya Babba har da kullawa a leda,sai bayan sallar magariba suka tashi zasu tafi,nan kuwa ta saka kuka ta riƙe Amina da Salma,suma kuma kukan suka saka dan ba ƙaramin tausayi ta basu ba,dan har yanzun jikinta da ɗan zafi,kuka take sosai tana roƙonsu akan kar su tafi su barta, Yaya Babba ce ta fisgesu"ke bansan Iskanci,kowa da kika gani haka aka masa,kuma yana ji yana gani yake rabuwa da dangin sa,yanda naga kina da wannan taurin kan wallahi ki kama kan ki,idan ki kaje kika yi abinda zai saƙo ki gida to wallahi kinsan halin uban ki, Gara ki kama kan ki,kai ku tashi mu tafi mana munafukai " Duk tashi suka yi suka fita sumi_sumi suna waiwayenta har suka bar gidan. Su Muha ne suka kai mai da su har sai Kofar gida,yayin da Ɗan Alhaji ya ba Yaya Babba dubu goma,Aunty Rahima dubu goma,Aunty Amina dubu goma,sai Salman da take kawar Amarya basu ma san ko nawa aka bata ba, Ko kofin ma su gama juya kudin harsun ja mota sun wuce, Ikon Allah,ba karamin mamaki da jin daɗin suka yi ba,haka suka rinka faɗa wai Abokin mijin Sumayya ya basu kuɗi,yaya Babba har da cewa Ohh dama ace shi ta aura ai da sun haye, Su kuma yan tarbar Amarya su Yaya Babba na wucewa suka kara share gidan tas suka kintsa komai kafin su tafi,dan mota biyu manya aka masu haya wanda zai kai su har cikin Ruga,suma kuma Ɗan Alhaji ya masu abin arziki sosai wanda yasa ba karamin daɗi suka ji ba,dan ko da suka zo sun tadda manyan kulolin abinci ne daga cidan su ɗan Alhaji. Bayan tafiyar su ne taji gidan ya mata shiru sosai,yaye lullubin dake kanta tayi tare da share hawayen fuskarta tana kare ma dakin kallo, Dakin gabaɗaya yaji tais sai katifar da take zaune a kai,sai Aƙwatin ta dake gefe,babu durowar saka kaya balle gado,kai koda ɗakinta na gida gadon sun tsufa amma dakin yafi wannan kyau,dan wannan yanda kasan dakin Tazuro haka yake *🍂JAURO🍂* (MAI ANGUWA) Story & Writing By JIDDARH UMAR 🌟🌙🌙🌙🌙🌙🌙🌟 *🌙✨MOONLIGHT WRITER'S ASSOCIATION🌙✨* https://m.facebook.com/Moonlight-writers-association-109698351308376/ *'''We are the moonlight writers we shine all over the world.''🌍'* ✍️✍️ بِسم الله الرحمن الرحيم ~~~~~~~💞💞~~~~~~~ *Ban yarda wani ko wata su saka min littafi a shafin su ko su mai da min littafi Audio ba tare da izini na ba* *29* *Wannan littafin nawa mai suna a sama na mai da shi na kuɗi,tare da Yar Tsanar Zinare,wanda yake son guda ɗaya dari uku 300,guda biyu 500 dari biyar, Hauwa Umar,Zenith Bank,2284905309,sai shaidar biyi ta wannan number 08141644865* *not edit* A hankali ta sauko daga saman gadon tamkar mai tsoron taka kasa haka ta nufe falon, Shima dai Babba ne sosai dan zai iya cin kushin saiti daya har da ƙari,sai dai babu komai a cikin shi,ajiyar zuciya ta sauke ta koma cikin dakin dan tana son tayi sallar Isha'i wanda bata samu tayi ba, Bandakin ma a wanke yake tas,sai dai daga dukkan alamu an saka mashi sabon tas ne,ga kuma botikan wanka harma da ƙaramin famfo a ciki, Kunna fanfon tayi ta tara buta sannan ta daura Alwalah,tayi sallar, Bayan ta idar ne ta kwonta a nan saman dardaman,dan yafi mata sauƙi akan ta kwanta kan wannan gadon, Koda aka zaunar da ita dazu daurewa kawai take yi,domin bala'i zarni yake,ga filo duk warin miyan barci,kai Allah yama Maman Momy yanda taso tayi da ita, Jin an buɗe ƙofar an shigo da sallamah ne yasa ta kara rufe ido zana lunkumewa gabanta na faɗuwa jin muryar shi,Allah yasa ba zai ce mata komai ba,dan wallahi ba zata taba yarda da mutumin da bata so ba, Jinshi tsaye a kanta ne yasa ta kara matse ido, "Ni dai nasan ance idan kayi aure da kashigo dakin matarka zaka ganta zaune saman gado da lulluɓi tana jira ka yaye mata,to ni me yasa na ga tawa a kwance,kenan hakan na nufin a shirye take jira kawai take na fara cire mata kaya" Wani irin zabura da tayi tana mikewa zauna har tana bangaje shi,domin yana kusa da ita ne a tsaye, Da sauri ya matsa baya yana kallon ta baki buɗe, Matsawa baya tayi tana kyara zaman hijabin jikin ta, Bata fuska yaye"ke me haka,wai ni ya na ganki haka ne Sumi Baby? Harara ta zuba mai,tana kauda kai, Ajiye ledan dake hannun shi gefe yayi ya shiga bayi,mintuna kaɗan kuma sai gashi ya fito,kallon ledan daya ajiye yayi,yana nan yanda yake,fita yayi sai gashi kuma ya shigo da plate a hannun shi,ajiyewa yayi ya buɗe ledar tare da fitowa da lafiyayyen gasasshen kaza wanda ya ji kayan lambu, Ɗaukar plate ɗin yayi ya ajiye mata a gabanta tare da zama ya na fuskantar ta,"ga nama ki ci sai ki sha magani"ya fada yana buɗe mata goran drink. Duk da tana jin yunwa amma ita ba mahaukacin kare bane ya cije ta da zata ci Kazan Amarci,"ba zan ci ba" Ɗan shiru yayi na ɗan wani lokacin yana kallon ta kamar mai nazarin ta,sai kuma yace"ki kwantar da hankalin ki ba abinda zan maki,tunda ba kida lafiya,bancin haka na san ma da kanki zaki nime ni in dai ni ne" Cikin jin haushin maganar shi tace"Allah ya tsare ni in nimeka da kai na" "Oh haka kike gani?to karki manta na faɗa maki ni bana ra'ayin zama da mace na har abada,da zaran kin haifamin yara biyu zuwa uku zan sallame ki na riƙe ya'ya na" Wannan karon juyowa tayi da kyau tana fuskantar shi cikin mamaki tace"to me yasa ka aure ni in ba kason zama dani har abada " "Saboda ya'ya na" "Wasu Ya'ya? ," Wanda zaki haifar min,kin ga,shi yasa nace ki kwantar da hankalin ki in dai ni ne,duk lokacin da kika shirya bari na,ko kika samu wanda kike so,to ki haifamin ya'ya na biyu ko uku sai na sallame ki" "Ta yaya zan haifa maka ya'yan? Ba kunya yace"though sexual mana,kuma ko yaushe kika tuntube ni a shirye nake,dan yanda kika ganni bugu daya zan maki ki dauki dana ko yata,ni ko yanzun kika shirya duk da ba'a shirye nake ba zan iya Kokartawa" Harara ta zuba mai tana ƙara matsawa tare da matse ƙafarta, Ganin yanda ta haɗe kafa ta na hararan shine yasa ya saka dariya"kin ga Sumi I am just joking,wasa nake yi babu abin da zan maki,amma maganar gaskiya sai kin nime ni da kanki " "Har a bada" "Zamu gani" Ya faɗa yana mikewa tare da faɗawa kan katifa, "Ummm umm"ya faɗa yana mikewa da sauri daga kan katifar da ya hau, " Sumi me ke wari haka"ya fada yana nuna mata katifar, Kin bashi amsa tayi wanda ganin hakan ne yasa ya yaye zanin gadon gabaɗaya ya tsaya yana kare ma katifar kallo, Dafe ƙwanƙwaso yayi yana jinjina kai, "Sumi bazan iya kwanciya akan wannan abun ba,ke ma sai dai kiyi haƙuri dan ba zan bari ki kwanta a ƙazanta ba,this is bad" Ɗaukar katifar yayi ya fitar dashi falo ya jingine,sannan ya dauko babban tabarma ya shimfida tare da shimfida zamin gadon a sama,kallon wurin yayi yana bata fuska "kai ina,gaskiya ba zan iya kwana a kasa ba Sumi" Ya fada yana kallon ta, Ganin ba tada niyar bashi amsa ne yasa ya ciro wayar shi dake Aljihu yana danne danne ya fita, Ajiyar zuciya ta sauke tana addu'ar Allah ya sa ya bar gidan ne,sai dai ko mintinu biyar ba'a yi sai gashi ya kuma shigowa, "Sumi kici wannan kazar mana,gashi tana hucewa" "Bazanci ba" Wannan karon babu Alamar wasa a fuskar shi yace"ba dan ni na siya ba kuma ba dan ki ci ki baya ba na siyo,domin ni ba na cin naman kaza,kuma ba zan yi asaran kudi na ba,idan kuma har ba ki ci ba to wallahi kinga can"ya nuna mata saman tabarma"to sai ya mana kaɗan ni da ke,na baƙi minti goma"yana gama fadar haka ya juya ya fita. Tabbas a yanda taga yanayinsa da gaske zai aikata abinda ya faɗa,kallon tabarman tayi,wane ita,haka kurum taurin kai ya ja mata bala'i. Jawo plate din tayi ta saka hannu a hankali ta fara ci,tun tana ci a hankali har ta buɗe ciki ta ci dayawa dan wanda ta ci yafi rabi,sannan tasha lemun tana jin wani irin sanyi a zuciyar ta,domin abinci ma rahama ne, Shigowa yayi ya kalle ta ya kalli plate ɗin "tashi muje" A tsorace tace"ina? Dafe goshinshi yayi"please Sumi na gaji tashi muje mu nime wurin kwanciya gobe ina da aiki bana son taurin kai I know you know that I will never hurt you"juyawa yayi ya fita yana ɗaukar wayar shi dake kara,taji dai yana faɗin gani nan fitowa. Mikewa tsaye tayi tana jan tsaki,"to ni kuma ko ina zai kai ni,ko dai yaya ne ta Allah ba taka ba,da wani broking English din shi "ta faɗa tana fitowa, Ganin baya falo kuma baya tsakar gidan ne yasa ta fito kofar gida in da ta ganshi tsaye jikin wani hadadden mota baƙi wanda daga dukkan alama sabuwa ce dal Yana ganin fitowar ta ya katse kiran da yake yi tare da mai da wayar Aljihu ya buɗe mata gidan gaba tare da faɗin Bismillah" Kallon shi take tana kallon motar cikin mamaki,wannan kuma motar waye,sannan ina zasu je, Sai dai babu me bata amsa kuma bata son ta bada kanta ta hanyar tambayar shi,dan kar yaga kamar tsoron shi take,shi yasa a hankali ta tako ta shige yayin da ya maida kofar motar ya rufe,shi kuma ya zagaya ya shiga mazaunin direba tare da tada motar yana mata key, Sam bata zata cewa shine zai ja motar ba,dan bata da tabbaci akan iyawar shi,cikin tsananin tsoro ta damki hannun shi dake saman giyar motar,tana waro ido tare da fadin..... *🍂JAURO🍂* (MAI ANGUWA) Story & Writing By JIDDARH UMAR 🌟🌙🌙🌙🌙🌙🌙🌟 *🌙✨MOONLIGHT WRITER'S ASSOCIATION🌙✨* https://m.facebook.com/Moonlight-writers-association-109698351308376/ *'''We are the moonlight writers we shine all over the world.''🌍'* ✍️✍️ بِسم الله الرحمن الرحيم ~~~~~~~💞💞~~~~~~~ *Ban yarda wani ko wata su saka min littafi a shafin su ko su mai da min littafi Audio ba tare da izini na ba* *30* *Wannan littafin nawa mai suna a sama na mai da shi na kuɗi,tare da Yar Tsanar Zinare,wanda yake son guda ɗaya dari uku 300,guda biyu 500 dari biyar, Hauwa Umar,Zenith Bank,2284905309,sai shaidar biyi ta wannan number 08141644865* "Ba dai kai ne zaka ja motar ba? Kallon hannun ta dake saman nashi yayi," Baki yarda da mijinki bane? Da sauri ta jinjina kai alamar eh, "Kenan kin yarda ni mijinki ne" Ya fada yana sauke hannun shi dake saman key din motar ya daura saman nata ya shiga shafawa a hankali,yana wani tsare ta da ido, Da sauri ta zame hannun ta daga saman nashi tana sai_saita zamanta"har abada " Bai bata amsa ba ya kara tada motar ya shiga tukawa a hankali yana kallon yanda ta lumshe ido bakin ta na motsawa a hankali,daga dukkan alamu addu'a take yi, Sai da ya fita cikin unguwar ya hau saman titi sannan ya shiga sharara gudu da ita kamar zai bar gari,saboda dare ne ba cikowar ababen hawa, Sai ta ɗan buɗe ido kamar zata mai magana sai ta maida ta rufe dan bata son raini, Ji tayi ya ce a hankali ya kara rage gudun kafin kuma ya faka motar a wani wuri, A hankali ta buɗe ido tana kallon in da suke,wani babban Store ne ya tsaya wanda taga an rubuta B.Y "Kina buƙatar wani abu,na ci ko na sakawa? Girgiza kai kawai tayi, " Ok to ina zuwa"ya fada tare da fita daga cikin motar,ya shiga Store ɗin, Ya kai mintuna goma sha-biyar kafin ya fito wani na binshi da manyan ledoji a hannun, Buɗe but din motar yayi yaron ya saka kayan a ciki kafin ya rufe,bata san ko nawa ya ba yaron ba,ta dai ga ya ciro kuɗi ya mika mashi, sannan ya shigo motar, "Sorry Madam Jauro"ya fada yana ta da motar,ta dauka babu nisa,amma sai gani tayi yana ta zura gudu,tun tana kallon hanya har ta gyara kanta ta fara barci dan ba ƙaramin gajiya tayi ba, Daga Unguwar Tunga inda aka kai ta zuwa Bosso Road ba karamin tafiya ba ne,sai dai ba Bosso yayi da ita ba yankan hanya yayi ta Bahago ya bullu dasu ta Zarumai sai gasu a wani Katafaren Hotel mai suna MATASA, Hon daya yayi me gadin wurin ya buɗe mashi ya shiga da motar, Har yayi parking bata sani ba,dan haka fita yayi daga cikin motar ya shigar cikin reception,sai da ya gama komai ya biya kudi ya amsa key sannan ya fito ya dawo in da ya bar ta, Kashe motar yayi sannan ya zagaya in da take, Tsayawa tayi a gabanta bayan ya buɗe motar, Ajiyar zuciya ya sauke yana ƙare fuskarta kallo,Sumayya fara ce sosai irin tas dinnan,sai dai kuma rashin wadata shi ya ɓoye kashi saba'in daga cikin kyan da Allah ya mata, Murmushi yayi ya saka hannu a hankali ya fito da ita ya mai da ƙofar motar ya rufe da ƙafa,sannan ya fara taku da ita tamkar wanda ya dauko yarinya karama,bawai kuma dun baya jin nauyinta ba,a'a sai dan jikin shi ya saba da aikin wahala kuma yana da juruya shi yasa,dakin su shine na 75,dan haka da yana buɗe ƙofar ya kwantar da ita saman kushin,ya kyara mata kwanciya sannan ya fita, Ba jimawa kuma ya kara shigowa da waɗannan Ledojin dazu ya ajiye a gefe ya koma ya kulle ƙofa, Toilet ya shiga yayi wanka,yana fitowa ya ɗauki waɗannan Ledojin ya buɗe,dogon wando da riga mai dogon hannu ya ciro sabo fel a cikin ledan,ya saka,sannan ya fito falo in da take kwance, Dakin da ya kama babban dakin VIP domin babban falo ne harda kicin a ciki,da kuma dakin barci,babu abinda babu a dakin, Tsugunwa yayi a gaban ta yana kallon yanda take barci cikin kwanciyar hankali,saboda dazun a asibiti an mata har da Alluran barci, Yasan taji daɗin barcin nan amma dole ta tashi ta yi wanka sannan ta canja wannan kayan, Cikin barcin ta mai daɗi aji kamar ana tsotsar mata baki,kara gyara kwanciyar ta tayi ta juya tana fuskantar sama, Ita bata masan wata damar bane ta bashi,dan haka hayewa yayi samanta ya mata runfa, Yayin da ya saka harshen shi a ƙarshen labbanta da kuma Gum dinta yana mata tafiyar tsutsa da tsinin harshen shi a wurin, Jin wani abu na bin ƙwaƙwalwar kanta yana yawo a sassan jikin ta ne yasa tayi wani irin mika tare da mirginawa,ai kuwa sai gasu a ƙasa sun fado yayin da ita ke kwance saman jikin shi,domin dama ba wai ya hau saman jikin ta bane dafa kushin din yayi shi yasa da tayi mika suka faɗo, Duk da saman jikin shi ta faɗa amma sai da ta danji zafi,dan haka da sauri ta buɗe ido tana kofar tashi,tare da kiran sunan Allah, Ji tayi an riƙe mata Kwankwaso wanda hakan ne yasa ta kalli kasa, Zabura tayi da sauri ta Mike tsaye tana waro ido "me kamin? Mikewa tsaye shima yayi yana dafe baya" Ko dai me kika min,"sai kuma ya saki murmushi yana kallon ta,"na doge Baby Sumi " Tsoro ya fara bata"dame fa"ta faɗa ita ma tana tsare shi da ido. "Oh bakisan me kika min yanzun ba? " Me na maka? Dan dariya yayi yana kallon ta,"dama bayan mun iso ne naga kin yi barci,to shine na dauko ki na shigo da ke,ni kuma naje nayi wanka na shirya kamar yanda kika gani,ina fitowa falo domin ta da ke kiyi wanka shine fa kawai naga kin tashi kin rungume ni kin shiga kissing dina kina wani shafa ni, Ihun da tayi ne ya katse shi,"wallahi karya kake min,ni ne na shafa ka har nayi kissing ɗinka,wallahi ba hali na ba ne,ya aka yi to na ganni a saman ka"ta faɗa cikin muryan tashin hankali da kuka, Shima waro mata matsakaitan idanun shi yayi"to ai ke kika danne ni,ni kuma ina ƙoƙarin tashi,Allah ya so ni so kika yi fa kiyi Repping dina ki min fyaɗe," Da gudun ta kara so in da yake tsaye ta shiga dukan shi da hannun ta a kiji tana saka kuka "wallahi karya kake min,sai dai in kai ne kake son kamin fyaɗe,kuma sai na rama sharrin da kamin" Bai dakatar da ita ba sai ma cewa da yayi "ni ne fa wanda ya kama yace zai rama,har balle kissing dina da kika yi ba tare da kin ni me izini na ba,ina iya yafe ko wanne amma banda wannan" Kafin ta samu abin faɗa mashi sai ji tayi ya dago habarta tare da saka bakinshi cikin nata ya shiga bata wani irin rikitaccen sumba mai tafiya da ilahirin gangan jiki,domin kuwa ya riga ya yasan duk wani tsirri na jikin diya mace lungu da saƙo inda zai taɓa ko ya sumbata jikinta ya motsa,haka kuma acikin baki yasa in da jijiyan sha'awar ɗan adam yake wanda ta hanyar sumba kawai zai kai saƙo zuwa ƙwaƙwalwa ita kuma ta harba zuwa gangan jiki, Hannu biyu ya saka ya rungumeta ta baya yayin da ya zagayeta da hannayen shi,yana ƙara tura harshen shi a cikin bakin ta, Tun tana dukan shi da hannun ta har taji jikinta ya mata wani irin sanyi kafafuwanta na nimar gaza daukarta,sai dai yaki bata damar zubewa ƙasan, Sai da yaga tana shirin shede mashi sannan a hankalin ya zare harshen shi daga cikin bakinta yana haɗa goshinsu wuri ɗaya yayin da Lebanshi ke saman nata yana busa mata numfashin shi tana shaka, Bai sake ta ba sai da ya kai ta kan kushin ya zaunar da ita, Sai lokacin ta samu damar fashewa da kuka ta ɗauki daya daga cikin filon kushin ta wurga mashi,ta kasa bayan hannunta tana goge bakin ta dashi"Allah ya isar min mugu mai danne ya'yan mutane" Dafe bakin shi yayi "kai_kai_kai ni ne mai danne ya'yan mutane,to bari in fara ta kanki" Ai kuwa gani tayi yayi kanta gadan_gadan da gaske kara danne ta zai yi, Hakan ne yasa ba shiri ta mike da gudu tayi cikin ɗakin,shima kuma bai tsaya ba da yake yayi niyar yin mugunta dan haka tuni yabi bayan ta da gudu, Tana juyowa baya ta hange shi yana binta,ai tuni ta kara gudu yana biye da ita abaya yana dariya ita kuma tana ihu,nan fa suka shiga zagayen wannan babban falon,su ne har cikin Uwar ɗaki, Sam ba tada jimirin gudu zagaye hudu ta faɗa kan gado tana ishi, Gadawo kanta tayi "wa na kama" Kauda kai tayi tana nishi, Juyo da kanta yayi suna fuskantar juna "ni kike ma Allah ya isa?......... *🍂JAURO🍂* (MAI ANGUWA) Story & Writing By JIDDARH UMAR 🌟🌙🌙🌙🌙🌙🌙🌟 *🌙✨MOONLIGHT WRITER'S ASSOCIATION🌙✨* https://m.facebook.com/Moonlight-writers-association-109698351308376/ *'''We are the moonlight writers we shine all over the world.''🌍'* ✍️✍️ بِسم الله الرحمن الرحيم ~~~~~~~💞💞~~~~~~~ *Ban yarda wani ko wata su saka min littafi a shafin su ko su mai da min littafi Audio ba tare da izini na ba* *31* *Wannan littafin nawa mai suna a sama na mai da shi na kuɗi,tare da Yar Tsanar Zinare,wanda yake son guda ɗaya dari uku 300,guda biyu 500 dari biyar, Hauwa Umar,Zenith Bank,2284905309,sai shaidar biyi ta wannan number 08141644865* Kyaf_kyafta ido ta fara cikin tsoron abinda zai iya zuwa ya dawo,domin yau din gani take gaba ɗaya ya canja mata kamar ba shiba,"dan Allah kayi haƙuri ka ɗaga ni ba zan ƙara maka Allah ya isa ba" "Kin tabbata" "Eh,na tabbata" Ɗagata yayi " Ki shiga banɗaki gashi can kiyi wanka ki canja kaya,ki duba a kwai kayan bacci a wancan ledar,karki manta kiyi brush sannan ki dauro Alwallah,bana son cin musu,idan kin kammala ki hau kan gado ki kwanta,karki bari na maimaita abinda na faɗa " Ba ta bashi amsa ba ta tashi ta shiga bandakin domin dama fitsari take ji tun a can gidan, Kamar yanda ya faɗa haka din tayi domin ta lura a lokacin da yaso wasa zai yi a lokacin da kuma yake baka umurni to kabi kawai sai ka zauna lafiya, Tana cire kayan daga leda banɗaki ta kuma shiga danta canja,tana addu'ar Allah yasa ba ƴan iskar kaya ya dauko mata ba, Ai kuwa ga mamakinta sai ganin irin kayan jikin shi tayi,sai dai nata yafi shep saboda na mata ne,riga wadatacce mai dogon hannu sai wando har kasa,kayan ruwan hanta ne,kuma yadin nada kauri sosai,sai hula da takalmin yawo a daki wanda a nan ta same shi, Baya cikin dakin dan haka a hankali ta tako ta leka ko yana falow kila a can zai kwana, Sai dai a zaune ta same shi yana kurban Liptop a karamin kofi yana kuma danne_danne a Laptop, Komawa cikin dakin tayi ta haye saman gado tare da jan baro ta rufe,tana tunanin kila gobe zai mai da ma Baba da katifar ne a canja wata,in ya so sai su koman, Tun tana tunani kar tayi barci ya shigo mata,har ba ta san sanda wani barci mai bala'in daɗi ya dauketa ba yayin da sanyin AC ke kadata. Washegari da Asuba jin sanyi ya mata yawa ne yasa a hankali ta buɗe ido tamkar wacce bata son buɗewa, Tozale tayi dashi a zaune saman gadon yana sakar mata murmushi"Sumi Baby tashi lokacin sallah yayi" Da sauri ta mike zaune tana tuna in da take, Sauka yayi bai kuma ce mata komai ba ya koma saman darduma yana cigaba da jan carbin shi, A jiyar zuciya ta sauke kafin ta sauko daga saman gadon tayi banɗaki,tana kiran Maye a zuciyar ta,dan ba ƙaramin haushi ya bata ba, Sai da ta kuma yin wanka sannan tayi sallah,ta zauna tana lazimi har ƙarfe shida da rabi sannan tayi addu'a, Juyowa tayi ta kalli in da yake zaune a saman karamin kushin yana haɗa wasu takardu gabaɗaya hankalin shi na wurin,dan haka tashi tayi ta hau saman gado ta kwanta tana lunshe ido, Bata ji takunshi ba,sai ji tayi an kwanta kusa da ita,wanda hakanne yasa da sauri ta bude ido tare da mulmulawa ƙarshen gado,tana shirin sauka, Ji tayi ya riko hannun ta da sauri shima ya fiskota da ƙarfi,ai kuwa sai gata kwance saman kirjin shi, Mirginawa yayi da ita sai gasu sun koma tsakiyar gado yayin da shi kuma yake kanta ita kuma tana kasa, Kollon cikin idanunta yayi yayin da ita duma ta kauda kanta a kanshi,dan haka kawai taji bata son kallon ƙwayar idon shi,dan gani take yana mata wani irin kallo na daban wanda yake sata jin wani iri,shi yasa tun jiya bata cika son haɗa ido dashi ba, "Nasan a gida kafin a kawo ki an sanar dake ni ne a sama dake kamar dai yanzun,me yasa baki gaishe ni ba? Ƙoƙarin ture shi daga kanta take yi sai dai ta kasa,wai meke damun Jauro ne,gabaɗaya sai ya dinga yin abu kamar bashi ba," Ɗan Allah ka ɗagani bana son kana taɓa ni" Hannun shi da ya mata katanga dashi ya zame,ai kuwa sai gashi kwance a jikin ta, Jin ya sakar mata nauyi ne yasa ta saka ihu da karfi,tana kiran wayyo Allah zan mutu, Daga ta ya kuma yi,"zan sauke maki nauyi na gabaɗaya nest time idan baki gaishe ni ba Sumi you can try it and see "ya na gama faɗar haka ya ɗaga ta,sai kuma ya juyo"ki yi kwanciyar ki dan ba abinda zan maki,kar ki manta na ce sai kin nime ni da kanki" Ya koma gefe yayi kwanciyar shi tare da jawo bargo ya rufe,(ni kuwa cewa nayi anya wanga ni ma da Jauro je kira mata bai shirya mata wani abuba) A hankali ta sauka daga saman gadon ta koma can saman ƙaramin kushin ta takure tare da lullubewa da hijabinta,dan ga sanyi gari ga na AC da Jauro ya kunna. Yana jinta amma bai kulataba,tun yana jin juye_juyenta har ya ji tayi shiru alamun barci ya kuma ɗaukar ta, Sauka yayi daga saman gadon ya ɗauki karamin filo ya daga kanta ya saka mata,dan ba ya son ya tashe ta, Shima komawa yayi kan gadon ya kwanta kafin wani barci mai daɗi ya dauke shi,dan jiya duk yanda ya so yayi barci bai samu yayi ba saboda project din shi da yake haɗawa, Yayi barci sosai kam dana ƙaran wayar shi ne ya tashe shi, Tunda yaga kiran Director na asibitin yasan aiki zasu saka shi bayan sun san yana kan hutun ne. Sai da yaja tsaki kafin ya ɗauka "barka da safiya yallabai" "Barka dai Dr, Sorry na tada kai daga dukkan alama" "Ba damuwa" "Nasan kana kan hutun ka ne,amma duk da haka muna bukatar tai makonka is an emergency situation" "Ok sir ganinan zuwa" Ya faɗa yana kashe wayar tare da sauka kan gado yana miƙa,banɗaki ya shiga yayi wanka sannan ya fito ya canja kaya ya fita tare da jawo kofa, A reception ya tsaya ya faɗa masu irin abincin da zasu kai mata nan da karfe goma dai_dai sannan ya wuce. Ba ita ta farka ba sai kusan ƙarfe goma sha ɗaya na safe, Miƙa tayi ta godewa Allah,lellekawa tayi ko ina sai dai baya nan,hakan yasa ta koma bayi ta wanke baki tana hamma,dan yunwa take ji, Ji tayi an ƙwanƙwasa kofa an shigo,kallon matar tayi wanda daga dukkan alamu mai aiki ce saboda harda irin kayan da masu aiki ke sawa a jikin ta, Da murmushi a fuskarta cikin harshen turanci take gaida ita tare da sanar da ita sau uku tana lekawa amma bata tashi ba tana barci, Ɗan keken da ta shigo dashi mai dauke da farantaiyen ta tsayar a gefe sannan ta shiga sauke mata abinci,tana kammalawa ta ce "Madam zan iya shiga ciki in gyara dakin tare da wanke bandakin" Ce mata tayi ta shiga,ita kuma ta jawo plate din tana buɗewa,wani irin soyayyen kwai ne wanda take ganen irin wannan suyar a wurin turawa,abu fari kar ba'a kife shi ya soyuba ga Yellow din ma har wani rawa yake alamar daka taɓa ruwan ciki zai fito,da sauri ta jayeshi gefe,ta dawo dayan,shi kuma ɗan yankan kankana ne karami wanda bai wuci loma biyu ba sai Apple madaidaici guda daya, Ji tayi kamar ta fashe da kuka,hango fulas ɗan ƙarami da kofi ne yasa ta jawo shi,tana addu'ar Allah yasa koko ne a ciki,sai dai tana tsiyayawa taga ruwan Liptop ne a ciki,sai dai kuma sai kamshi mai daɗi yake fitarwa,hakan ne ya ja ra'ayin ta harta sha Liptop din wanda sai da ta juye duka karamin fulas din kofi biyu kenan,tas ta shanye amma ji take kamar ruwa kawai tasha, Jawo plate din da Kankanan yake tayi,to shine ma data ci taji cikinta ya ɗan daga amma kaɗan, Dan maganar gaskiya ta saba a gida ta ci malmala biyu na sauran tuwo da safe,in kuma Koko ne sai ta cika babban kofin silba,amma dan rai nin wayau shine yanzun Jauro zai haɗa ta da kayan kwalama a matsayin abin kari,gaskiya ba zata iya ba,ba tada jimirin yunwa, Matar na fitowa ta dakatar da ita,cikin harshen Turanci take tambayarta "zan iya samun wani abinci bayan wannan? " Eh me kike so" Kallon Agogon bango na falon tayi,shadaya tayi"zan samu Sakwara da miyar ganye " "Eh zaki samu,muna da ferfeson kifi dana rago,harma da kayan ciki,wanne kike so? Nan take ta sake fuska ta shiga sakin lallausar murmushi" Ki kawo min ferfesun kifi,ki hado da lemu mai sanyi " "An gama ranki ya daɗe" Ba jimawa kuwa sai ga matar dauke da abinci a babban tire ta kawo mata komai kamar yanda ta faɗa,"Madam kudin abincin zaki bada yanzun ne ko a saka a lis dinku? To ita ina taga kuɗi,"A saka a list in yazo zai bada " "Yes mah" Matar ta fada tana barin dakin dan bata damar cin abincin ta. Kyara zama tayi da kyau bayan ta sauko kasa a haucin abincin ta hankali kwance,sai da ta cinye sakwaran tas da miya harda lashe kwano,farfeson kifin ne dai duk yanda ta so ta cinye ta kasa saboda irin ƙoshin da tayi, Ko mikewa ba tayi ba,ta ji an buɗe kofa an shigo, Kallon_kallo aka shiga yi tsakanin ta dashi,yana kuma kallon plate din dake jere a gabanta,ya kalli list din da aka bashi na kusan dubu takwas,shi tunda garin Allah ya waye bai zauna ya kashe ma kanshi dubu biyu ba,amma ita gashi zama daya taci dubu takwas,to wallahi ba dashi ba,dole ya fanshe kuɗin shi yau a jikinta,kuma yanzun a yanzun nan babu ɗaga ƙafa ko kaɗan, A hankali yake takowa yana nufo in da take zaune,yayin da yake raya abubuwa da yawa a kanta....... *🍂JAURO🍂* (MAI ANGUWA) Story & Writing By JIDDARH UMAR 🌟🌙🌙🌙🌙🌙🌙🌟 *🌙✨MOONLIGHT WRITER'S ASSOCIATION🌙✨* https://m.facebook.com/Moonlight-writers-association-109698351308376/ *'''We are the moonlight writers we shine all over the world.''🌍'* ✍️✍️ بِسم الله الرحمن الرحيم ~~~~~~~💞💞~~~~~~~ *Ban yarda wani ko wata su saka min littafi a shafin su ko su mai da min littafi Audio ba tare da izini na ba* *32* *Wannan littafin nawa mai suna a sama na mai da shi na kuɗi,tare da Yar Tsanar Zinare,wanda yake son guda ɗaya dari uku 300,guda biyu 500 dari biyar, Hauwa Umar,Zenith Bank,2284905309,sai shaidar biyi ta wannan number 08141644865* Tsayawa yayi a gabanta,"kin kammala?ya tambaye ta hankali kwance,domin ya riga ya shirya ma abinda zai mata, Ita ma kallon kwanukan tayi sannan ta kalle shi"umm " "Yayi kyau,yanzun me zaki yi? Wannan karon hararanshi tayi" Me kuwa zan yi,kamai da ni gida" Ajiyar zuciya ya sauke tare da tsugunnawa a gabanta "me yasa baki ci abincin da nasa aka kawo maki ba? " Saboda banga abincin a wurin ba sai ɗanyen ƙwai " "Amma dai kinsan cin irin wannan abincin mai nauyi da safe yana saka lalaci,dan yanzun na tabbata idan aka barki zaki iya niman wuri ki kwanta,wanda haka na iya buɗe ki cikin ƙanƙanin lokacin ki zama uwar mata,ni gaskiya bani ra'ayin mace me ƙiba,shi yasa ma na tsara maki times table na abincin da zaki dinga ci kar azo ki fi haka a kiraki da uwata," "Me kake nufi? " Tashi muje mutsa jiki" Kauda kai tayi "ba in da zanje" Mikewa tsaye yayi yana dariyar mugunta,tare da cire rigar jikinshi yana ƙoƙarin kwance belet din wandon shi, Zaro ido tayi"me zaka yi" "Abinda kike tunani" Mikewa tsaye take ƙoƙarin yi "Duk in da zaki shiga a dakin nan ba in da ba zan iya shiga ba,Gara ma karki wahalar da kanki" Har tana in_in_na "kaga tsaya,in dai Exercise ne muje wallahi a shirye nake basai ka cire kaya ba" Murmushin gefen fuska ya sake "A'a ni nafi son karki je,kin ga sai muyi na kan gado dama gashi kin koshi wallahi Sumi tuni zansa kiji wata yunwar"yana ci gaba da ƙoƙarin cire balet din, " To ba na ce zan je ba,dan Allah ka mai da kayan ka," Maida rigar shi yayi,da akwai abinda ya dawo dashi amma wallahi ya fasa,"tashi muje" Tashi tayi ta shiga daki ta canja kaya ta saka hijabi ta fito, Shi ya buɗe mata kofa suka fita sai cika take tana batsewa, bai dai kula taba har suka fito bakin titi, A tunanin ta tafiya zasu yi su dan zagaya sai su dawo,amma sai gani tayi ya tare Abin hawa "Mekunkele nawa zaka kaimu" Mai adaidaita yace"dari biyar " Kallon shi yayi sama da katsa"dari biyu " Mutumin bai ma bashi amsa ba ya ja adaidaitanshi ya wuce,dan ya lura wannan ɗan rainin hankali ne,ko dari uku ba zai iya zuwa ba balle wata dari biyu, Kara tare wani yayi,shima dari huɗu yace,amma yace sai ya bar mashi dari biyu,haka shima ya tafi basu shirya ba, Ita dai tana tsaye tana kallon shi gaba ɗaya takaici ya gama cika ta,amma ta san abinda zata mai,in dai takamarshi bai iya cire kuɗi, Yana tare na biyar ya ce maikunkele sabon Titi,taji mutumin yace shiga muje,kafin yace nawa harta zagaya ta shige ciki ta zauna, Kallon ta yayi"ke ai bamu shirya ba" Kauda kai tayi ni na shirya"malam nawa? "Hajiya bada ɗari shida" "Angama," Kallon shi tayi"ka shigo mana" "A'a wallahi ba da ni ba,ɗari shida fa,a ɗari huɗu banje ba sai a dari shida,kin ga fito,in dai bake zaki bashi kuɗin ba" "Kai dai ka shigo tunda kaji na yi magana ai ni zan bashi" Kallon tuhuma yake mata"ni fa ba zan biya ba" "Ohh God,ɗan Allah Jauro muje" Shiga yayi ba tare daya ce mata komai ba kamar yanda ita ma bata ce mashi komai ba duk da bata San in da zasu ɗin ba, Nan ma tafiyace mai nisa sosai,kamar zasu bar garin Minna,harda ɗan dajuka take gani kafin taga yace ma mutumin yabi ta can,mutumin nabi sai gasu a bakin wani katafaren gidan gona babban gaske wanda ita bama ta iya ganin ƙarshen katangar shi, Cewa yayi mutumin yayi parking a wurin,yana tsawa ta yi sauri ta fito ba tare da tace masu Komai ba ta doshi wannan Get din ta zauna a saman bancin da ta gani a wurin kafin ya gama biyan kuɗin mai Adaidaita wanda ta san sai ya dauki lokaci. Dukkanin su da kallo suka bita har ta zauna kafin mutumin yace"malama kuɗi na " Ɗan daga murya kaɗan tayi tana nuna mashi Jauro"ga mijina nan shi zai baka dan ni ba ni da ko sisi " Wani ashar ya dura sai da mai Adaidaitan ya kalle shi,"ni zaki rai na ma wayau,bayan kin ce ke zaki biya? Turo baki ta yi "to ban dashi,kawai ka bashi kudin shi mutafi," Kallon ta yake yama rasa ne zai ce mata, "Mallam sallame ni in tafi" Juyowa yayi"dan Allah ɗan uwa ka taimake ni na baka ɗari biyu mana,kaga banda kuɗi " "Kan uba,wallahi baka isa ba,ai babu in da zanje sai ka biyani kudi na" Jin zagin da yayi ne yasa cikin jin haushi yace"to wai ni na ce maka zanje,ina ce a gabanka ta yaudare ni tace in shigo zata biya,dan haka kaje can ta biya ka " Kallon sama da kasa ya masa"ai kuwa baka isa ba tunda matarka ce,dole ka biya ni," Ji suka yi tace "Malam riƙe shi kuɗi ne dashi kar ka yarda sai ya biya ka" "Hande min boni,Sumi Baby dama ke mumafuka ce ban sani ba?dake za'a haɗa baki a cuce ni" Kwalo ta mashi da harshe,ai shi ya dauko ta ba da son ranta ba,ai ya shiga uku ba dai ta gane kuɗi ne bai son kashewa ba,to ya shirya (a zuciya ta nace in dai Jauro ne ke ma kishirya shiga uku) "Wallahi ko dai ka ban kuɗi na kona maka saran kuɗi na" "Kai yaro ni Doya ne da zaka sare ni ko kuma ni kabewa ne,dena ganina haka tsaf zan yi maganin ka" "Ok haka ka ce ko" Mutumin ya fada yana daga kujerar gaba da suke zama,sai gashi ya ciro wata sharbebeyar Adda sabuwa fil har ɗaukar ido yake yi,yaci kwalan Jauro wanda bai lura da Addan, A fusace ya juyo "kai dan ub...... " Ganin Adda na daukar ido ne yasabai masan sanda ya duka ba"dan girman Allah ka yi haƙuri ni dama wasa nake maka,haba dari shidan me,kaga amsa"ya faɗa yana ciro yan dubu_dubu a Aljihunshi wanda a kalla sun kai dubu biyar, Ita kuma ganin Adda ne yasa cikin sanda ta tashi ta labe a jikin bangon tana leken su, Fisge kudin mutumin yayi duka"ɗan rai nin wayau dama kanada kudi ka tsaya bata min lokaci, Nan ya mai da Addan ya tada Adaidaitan shi ya bar wurin, Kallon fuskar shi kadai da tayi yanda yake haɗa zufa yasa ba ta san sanda ta shiga sheka dariya ba har tana zaunawa a katsa,tana kuma nuna shi da hannu, Idan ranshi yayi dubu to ya baci,sai dai shi ba akan dariyar ta bane dan ko akai baya kawo ta,haushin shi daya shine kuɗin shi da aka tafi dashi,tsaki yaja yana dusar Get ɗin,cikin jin haushi ya shiga dukan Get din da ƙarfi, Ai kuwa sai gashi wasu maza su biyu sun fito da sanda,daga ganin su Fulani ne, "Ai kin banza ni banga amfanin zaman ku a wurinan ba dan har a kashe mutum baku sani ba" Kallon ta yayi da tayi shiru tana kallon su,dan bata ɗauka ma wurin a kwai mutane ba, "zo mu shiga in kin gama kafin na fara nawa" A hankali ta tashi sannan tabi bayan shi suka shiga ciki tare, Ya na gaba tana biye dashi a baya tana kalle_kallen katon filin da suke ciki,sai da sukayi tafiya mai dan nisa kafin su iso wasu irin manyan dakuna masu faɗi da tsayi,wasu suna da raga kamar dai dakin kiyon kaji,sai dai kukan Talo_talo take ji wanda daga dukkan alamu rukakku ne,ta inda take tsaye ta ɗan leka,ai kuwa sune manya manya sukai guda Hamsin a ciki, Ji tayi yana ce ma wasu mutane su biyu da suke gai dashi"ina waɗanda zasu share ɗakin kaji? "Yallabai suna ciki yanzun zasu fara" "To kace su bar shi,yau su huta,mu zamu share" Kallon shi mutumin yayi ya kalli Sumayya da take ƴar gayu kuma dai yaji ance jiya mai gidan nasu yayi aure ba dai Amaryar ɓace wannan "ranka ya daɗe ka bari sun yi"ɗayan ya faɗa. Cikin jin haushin abinda Sumayya ta mai ya ce" Na ce ka bari zamu yi,dan Allah je ka sallame su"Da sauri suka juya suka tafi, "Muje ko" Ya fada yana sakar mata murmushi, Bata kawo komai a ranta ba ta bi shi Ire-iren wadannan gine-ginen sukai guda takwas a jere,biyu Talotalo ne a ciki,biyu kuma farafen kajin Agric ne,biyu kuma na masu ƙwai ne,biyu kuma na kosassun kajin gida ne,sai dai daya babu komai a ciki,shine wanda ya bude kofar ya shiga tana biye dashi, Da sauri tayi baya tana matsawa tare toshe hanci "wai wurin nan na wari gaskiya sosai," Kallon wanda ke biye dasu yayi"kawo mana kayan aiki," Da sauri mutumin ya juya,ita ma fita tayi ta tsaya ɗan nisa da ƙofar, Can kuma sai gashi rike da wani leda,mika mata yayi "ga kayan da zaki saka akwai Facemarks aciki saboda wari, Kallon rashin fahimta ta mai" Me kake nufi? "Motsa jiki" Kara maimaitawa tayi"motsa jiki kuma? "Eh" "A ina,me kuma sai na saka kaya in shiga wannan dakin mai wari,ta ina zan motsa jikin a ciki? " Oh kar dai ki ce har kin manta irin abinda kika ci,to wannan abincin da kika ci abincin dubu takwas kenan,to ni kuwa me zai sa na kashe maki dubu takwas da safe ba tare da kin min aikin komai ba,ni ma fa aiki na yi na samu kuɗin,dan haka dole na fanshe kudi na,kin ga wannan ɗakin na kaji,shi zaki shiga ki share tas,sannan za'a kawo maki ruwa da Omo sai ki wanke,yauwa sai kin yi da kyau dan sai kin saka faka kin ta kankaro kasa saboda kashin daya daskare,kwana biyu ba'a share ba," Wani irin kallo ta bishi dashi,"lallai ma Jauro,yanzun kai ko kunya baka ji ba,ina matsayin matarka kuma Amarya wacce aka kawo maka ita a daren jiya shine zaka kawo ni irin wannan wurin kawai dan na ci abincin dubu takwas " "To me aciki,kin ga kina ma bata ma kanki lokaci ne" Gyara tsuwarta tayi"idan na ce ba zan yi ba fa? Dafe Kwankwaso yayi"da na nuna maki kwanjina,dan wallahi idan na riƙe ki sai kin kasa tafiya" "Ba sai ka rike ni in gani ba"tana faɗar haka ta juya ta shiga zuba gudu tana dosar Get din da ko hangar shi ba tayi, Bin bayanta shima yayi aikuwa nan suka shiga tsere ita dashi a wannan babban filin,duk ma'aikatan da suka leko in dai sun ga shine tuni suke komawa bakin aikin su, Kawai dai baiyi niyar kamata bane yafi son sai ta gama ƙarar da Energy ta,ta yanda zai ji daɗin nuna mata kwanjin shi...... *🍂JAURO🍂* (MAI ANGUWA) Story & Writing By JIDDARH UMAR 🌟🌙🌙🌙🌙🌙🌙🌟 *🌙✨MOONLIGHT WRITER'S ASSOCIATION🌙✨* https://m.facebook.com/Moonlight-writers-association-109698351308376/ *'''We are the moonlight writers we shine all over the world.''🌍'* ✍️✍️ بِسم الله الرحمن الرحيم ~~~~~~~💞💞~~~~~~~ *Ban yarda wani ko wata su saka min littafi a shafin su ko su mai da min littafi Audio ba tare da izini na ba* *33* *Wannan littafin nawa mai suna a sama na mai da shi na kuɗi,tare da Yar Tsanar Zinare,wanda yake son guda ɗaya dari uku 300,guda biyu 500 dari biyar, Hauwa Umar,Zenith Bank,2284905309,sai shaidar biyi ta wannan number 08141644865* Tun tana gudu da ƙarfin har ta koma ji kamar mai da ita baya ake yi, Hakan ne yasa take ƙoƙarin tsayawa,sai ji tayi yayi sama da ita ya Daura ta saman kafadarsa yana tafiya da ita,wulle_walle ta fara yi da ƙafa tana dukan shi ta baya "ka sauke ni,ba in da zanje ni ba zan yi wani sharan kashin kaji ba,waiyo Allah ka sauke ni na ce" Ji tayi ya dire ta a saman wasu busassun ciyayi,wadanda aka tara da yawa aka jingine dami_dami, Ƙoƙarin mikewa take yi,da hannun shi ya mai da ita, Buɗe baki tayi tana shirin yi mashi wata tsiwar taji bakin shi a cikin nata,wannan karon ba irin Kiss din da ya mata jiya bane,na yau wani iri ne daban wanda ita sam bata fahimtar komai ba sai zafin da taji yana ziyartar lip ɗinta, Ƙoƙarin ture shi take yi amma sai ma ƙara manne mata da yayi,yana mata wani irin kiss kamar zai cire bakin ta gabaɗaya, Hannun shi taji yana turawa cikin rigar ta yana tafiya dashi sama a hankali kamar baya son zuwa, Sai zaro ido waje take ta rasa yanda zatayi domin ko motsi ya ki bata damar yi, Hannun ya tura a tsakanin bireziyarta kamar zai taɓa kirjinta,wani irin dauke numfashi tayi,kafin taji ya sauya akalar tafiyar ya gangaro da hannun ya tsayar akan ɗan ƙaramin ramin Cibiyar ta yana shafa wurin a hankali yana zagaya hannun shi a gabaɗaya Kwankwason ta,wani irin ajiyar zuciya mai sanyi ta sake jin bai kai in da bata son ya je ba, Cikin salon mugunta ya ɗan ja lip din kaɗan sannan ya saki ta yanda dole ta ɗan ji zafi, Ihu ta sake wanda ko fita bayayi,dan ji take makar ya haɗa ne da muryarta ya tsotse, Maida fuskar shi yayi saitin kunnen ta,yana sake mata nunfashe tare da bata light Kiss a wurin,"zaki yi aikin ko na ci gaba,please ki ce ba zaki yi,wallahi gida zamu tayi dan nan banga in da zai ishe mu ba" Numfashi ta har ji take kamar zai dauke wurin faɗin "zan yi aikin,sake ni zan yi,koma menene" Shafa wuyanta yayi"haba mana Sumi Baby,ki ce A'a" "Wallahi zan yi muje ka gani" Ajiyar zuciya ya sauke yana daga ta, Dan yamutse fuska yayi yana shafa mara"muguwa kawai,sai da kika wahalar dani sannan zaki ce zaki yi sharan,ai so nayi ki ce baki yi dana samu na rage abinda ke damuna"ya faɗa yana bata hanya, "Ai kaine babban mugu mara mutunci mai son kuɗi tsiya,in sha Allahu ba dai a kaina zaka rage abinda ke damuka ba,sai dai ta kashe ka" Ta fada a zuciyar ta tana tafiya tana shafa bakinta da taji kamar an shafa mata rop saboda yanda yake sulili,kai wallahi Jauro mugu ne. Tana tafiya yana biye da ita har suka iso kofar ɗakin,daukar ledan dazu tayi ta saka hand gloves da face marks ɗin sai dogon takalmi wanda da kyar ma take iya tafiya dashi, Tana kallon aka kawo mashi kujera ya zauna yana kallonta ta dauki tsintsiya ta fara sharan kashin kajin, Waiyo Allah wuri ne ba ɗan ƙaramin,gashi wani wuri ya daskare, Ko da tayi rabi ji tayi hannun ta da Kwankwason ta kamar zai ɓalle,gashi har ƙarfe daya saura, Kallon in da yake zaune tayi,yana kurban abu a kofi, Ajiye tsintsiyar tayi ta zo In da yake zaune ta tsaya tana kallon shi, Jin warin kaji na damun shine yasa ya dago ya kalle ta, "Ke lafiya" Turo baki tayi tana yin raurau da ido "na gaji" Ajiye kofin hannun shi yayi"kin gama ne"ya faɗa yana leka dakin daga in da yake zaune, "Na yi rabi" "Ai wallahi sai kin gama,yau kaɗai asaran nawa kika saka ni,ba zan biya wani kuɗi ba domin wasu su share min,kwanciyar hankalin ki shine ki share min ki zauna lafiya,shikenan" Bata San sanda ta fara hawaye ba,ɗan Allah ya gani ta kai makura wurin gajiya,in dai bata sauke girman kai ba ta bashi haƙuri tana iya yanke jiki ta faɗi, Da sauri ta karaso in da yake ta tsunguwa a gabanshi "dan Allah jauro kayi haƙuri,wallahi na gaji bazan iya ba" "Me suna na? Kai tsaye tace " Jauro " "Ni waye a wurin ki? Shiru tayi kamar mai tunanin amsar da zata bashi,yanda kasan mai ciyon baki haka tace" Kai miji na ne " Murmushi ya sake "good,to me yasa baki girmama ni,naga idan za'a kai ku gidan miji iyaye na maku fada akan ku girmama mazajen ku,duk abinda suka ce ku yi,wanda ba su so ku bari, An ya kuwa Sumi an maki irin wannan faɗar? Shiru kawai tayi tana kallon shi, " Fadamin gaskiya? Cikin sanyi murya tace"A'a " Dan zaro ido yayi harda dan buga cinya"yauwa,haba ai na sani,shi yasa biri yayi kama da mutum,kai amma gaskiya su mama basu min adalci ba tunda basu faɗa maki ba,shi yasa kika rai na ni " Ita dai burinta kawai ya mai da ita gida ta huta,dan haka ƙara marairaicewa tayi "dan Allah kayi haƙuri,ba zan sake ba" "No karki damu,Amma kin San abinda za'ayi? Da sauri ta girgiza kai tana murmushi, " Yanzun ki tashi ki fara ƙarasa sharan ki wanke wurin sai mu tafi,dan nima na fara gajiya"ya faɗa yana mika, Tuni ta nime murmushin ta rasa"please Jauro dan Allah,kaga ko gobe ne sai muzo na ƙarasa " Ɗan zaro ido yayi"ni!in salon ki sa ɗan Adaidaita ya sare ni,kinga i ki gama mu tafi malama " Ba yanda ta iya haka ta koma tana yi tana hutawa,tana hawaye har ta samu ta karasa da rarrafe, Bata ma iya wankewa ba amma ji take daga hannun ta har ƙafarta duk ciyo suke mata, Tana fitowa shi kuma yana dawowa daga sallar la'asar. Murmushi ya sakar mata"biyo ni" Bata ce mashi komai ba tabi bayan shi,dan ita yanzun ba tada bakin magana,dan ji take ko tayi ba zama aji me take faɗa ba saboda rashin Energy, Sun ɗan yi tafiya me nisa a ciki kafin su iso wani ɗan madaidaicin Flat Ganin ya shiga ne yasa ita ma ta shiga,falo ne mai dan girma yana ji kamar office ne,dan harda kujeru a ciki,zama yayi a kan daya tare da nuna mata wata kofa"ga banɗaki can ki shiga ki yi wanka,ga kuma kaya nan a leda ki ɗauka sai ki canja,dan ba zan iya bin hanya dake haka ba kina warin kashi" Bata ce mashi komai ba ta dauki ledar ta shiga banɗaki wanda taga an haɗa mata ruwan wanka har baho biyu duka masu zafi yanda zata ji daɗin gasa jikin ta, Ta jima sosai a bayin kafin ta kammala ta canja kaya wanda na yanzun riga da sike ne na Atamfa mai kyau kamar an auna jikinta,sai babban mayafi baƙi,harda mai a cikin kayan, Tana kammalawa ta buɗe ƙofar ta fito, Daga kai yayi ya kalle ta yana sakin murmushi "yauwa Sumi Baby ko ke fa,har kin fito a Amaryar ki," Tashi yayi ya zo gabanta yana jan hannun ta"nasan kina jin yunwa,ga abinci na sa an kawo maki " Jin yace abinci ne yasa ta bishi babu turjiya dan ba karamin yunwa take ji ba, Shinkafa ce fara da miya sai naman rago wanda aka saka yanka biyu manya, Kokarin daukar plate take ta zuba,ya amsa plate din a hannun ta"kawo na zuba maki" Tana kallo ya zuba madaidaicin chokali biyu,ya zuba miya da nama ɗaya a sama ya miko mata, Kin karɓa tayi ta noke, Ƙara Miko mata yayi"karɓa mana" Girgiza kai tayi tana turo baki "ni wannan yamin kaɗan ka ƙara min" "Wai me yasa kin cika ci ne,kin ga wallahi ko ki amsa ko na zauna na cinye,kuma in kika bari na cinye kin ma kanki dan ba zan siya wani abinci ba sai gobe kuma" Dan marairaicewa tayi kamar zata saka mashi kuka"dan Allah mana Jauro,ko kaɗan ne" Ganin yana ƙoƙarin mai da abincin gaban shi ne yasa da sauri ta amsa"kawo "ta faɗa tana turo baki,dan ji take kamar ta mangareshi da duka,ita wallahi tsakanin ta da Maman Momy Allah ya isa domin ita ta haɗa ta da wannan fitina. Haka tana ji tana gani ya kinkime kulolin ya fita dasu,ta jima tana juya abincin kafin ta daure ma zuciyarta ta shigaci a hankali,sai dai kwata-kwata bai wuce loma goma sha biyar ba da tayi abincin ya kare,Allah sarki Sumi harda kankare plate take, Shigowa yayi ya kalle ta ya kalli plate din,tabe baki yayi"tashi muje" Mikewa tayi tabi bayan shi,sai dai tana fito taga wata Arniyar mota ƙiran Jip sabuwa dal a fake, Gani tayi ya buɗe ƙofar motar ta baya "Bismillah" Ya mata nuni dashi, Ita fa tsakanin jiya da yau kaɗai wallahi Jauro lamarinsa ya fara bata tsoro,irin wannan manyan motoci fa,wannan ba irin na jiya bane daya kawo su,haka duk da bata san yanayin kuɗin Hotel ba amma ta tabbatar da ɗakin da suka kwana jiya ba karamin ɗaki bane,ita dai Allah yasa ba haɗa baki sukayi da shi da Maman Momy da Baba ba su saida ita, Tana shiga cikin motar shima ya zagaya ya shiga in da take,yayin da direba yaja motar suka bar wannan gidan gonar da bata fatan sake zuwan shi. A tunanin ta gidan su na jiya da aka kaita zasu koma,sai dai gani tayi an shigo dasu harabar Hotel din jiya, Hakanne yasa ta kalle shi,duk da ta ga idon shi a rufe amma ta san ba barci yake ba,"ina ce gida zamu koma" Kin bata amsa yayi kamar bai jita ba, Kara maimaitamai ta yi "na ce ba gida zamu koma ba? Ɗan buɗe ido kaɗan yayi" Hala dai ke kike biya min kuɗin daki,da zaki dame ni"gyara zama yayi da kyau yana buɗe idanun shi tar a kanta"me yasa wai ku mata kuna da matsala ne" Katse shi tayi"ai duk matsalar mu bamu kai na wani ba,mai kai matar shi Amarya sharan kashin kaji a yinin ta na farko tare dashi"ta fada tana kauda kai kamar ba ita tayi magana ba, Ɗan zaro ido yayi"me kika ce? Ita ma kin kula shi tayi,sai ma buɗe ƙofar motar da tayi ta fita ganin sun iso, "Zan yi maganin ki" Ya fada shima yana fitowa, Ta rigashi isa kofar amma saboda makulli na hannun shi dole ta tsaya sai da ya iso sannan ya buɗe ƙofar suka shiga, Faɗawa tayi kan kushin tana sauke numfashi tare ɗin "wash Allah baya na" Tsaki ya ja "mutum sai lalaci" Ita dai bata kula shi ba sai juye juyen da take yi kan kushin,dan ji take gaba ɗaya jikinta ciyo yane mata,har balle Kwankwaso, Yana shiga daki wasu takardu ya ɗauka ya ƙara fita, A nan kwancen da take tunanin Mama ya faɗo mata,yanzun ko a wani hali take,kila ma su Aunty Amina suje kai mata sauran kayan su iske gida ba kowa,Allah sarki Mama, A fili ta furta"ina kewarki Mama "haka dai ta zauna a wannan dakin ita ɗaya,gashi ba tada waya balle ya ɗebe mata kewa ko ta kira gida taji muryar su, Har aka kira sallar Isha'i tayi sallah bai dawo ba, Anan in da tayi sallah ta kwanta saman darduma,nan take kuwa barci yayi gaba da ita,wanda tana yi ne tana juye juye, Bashi ya shigoba sai kusan ƙarfe tare, Yana ajiye ledan da ya shigo dashi ya shiga banɗaki yayi wanka ya saka kayan barci, Kallon ta yayi yanda ta kwanta a kasa ta dunƙule da hijaba alamun sanyi take ji, Daukar rimot din AC yayi ya rage sanyi,sannan ya ƙarasa in da take kwance, A hankali cikin budara yanda ba zai tashe ta ba ya zame mata hijabin da ta rufe dashi, Filon da ya dauko ya saka a gabanta ya dan guyata sai ya kasance kamar ta rungume filon ne ta bashi baya, Hakan ne ya bashi damar zuge mata zip din rigar ta wanda ya tsaya iya Kwankwaso,ya zamana yana ganin fatar bayanta, Kallon farin fatar bayan nata yake wanda yake fari tas dashi,kamar mai maganar zuci haka yake kyada kai, Wani dan karamin gwangwani ya ciro a leda wanda daga dukkan alamu Oiltement ne na baya, Lakuta kaɗan yayi a tafin hannun shi ya mussuka sosai sannan ya shiga yi mata wani irin tattausar danna yana yawo da hannun shi a bayanta har zuwa Kwankwaso, Baiwar Allah,cikin barci taji kamar ana mata tafiyar tsutsa a baya mai daɗi ai tuni ta ƙara kifewa tana bashi damar Gara danna da ƙyau, Ganin abinda tayi ne yasa shi murmusawa, Ya dau tsayin lokaci mai yawa yana aikin danna mata jiki har zuwa hannayen ta da tafin kafarta,kafin a hankali ya kuma daukarta ya maida ita saman gado yana rufe ta da bargo,sai dai bai maida mata da zip din rigar ta ba kamar yanda bai cire mata rigar ba,ta yanda ba zai takura mata ba wurin barci....... *ASUBA TA GARI SUMI JAURO* *🍂JAURO🍂* (MAI ANGUWA) Story & Writing By JIDDARH UMAR 🌟🌙🌙🌙🌙🌙🌙🌟 *🌙✨MOONLIGHT WRITER'S ASSOCIATION🌙✨* https://m.facebook.com/Moonlight-writers-association-109698351308376/ *'''We are the moonlight writers we shine all over the world.''🌍'* ✍️✍️ بِسم الله الرحمن الرحيم ~~~~~~~💞💞~~~~~~~ *Ban yarda wani ko wata su saka min littafi a shafin su ko su mai da min littafi Audio ba tare da izini na ba* *34* *Wannan littafin nawa mai suna a sama na mai da shi na kuɗi,tare da Yar Tsanar Zinare,wanda yake son guda ɗaya dari uku 300,guda biyu 500 dari biyar, Hauwa Umar,Zenith Bank,2284905309,sai shaidar biyi ta wannan number 08141644865* Washegari da Asuba ta rigashi tashi,miƙa tayi tana karanto Addu'ar tashi daga barci, Ji take gaba ɗaya jikinta ya sake ba inda ke mata ciyo, Murmushi ta sake tana saukowa da ƙafarta a hankali ta mike sannan ta nufi banɗaki, Wanka tayi ta fito ta canja kaya,wanda a lokacin ne ya tashi, Kallon agogon dake manne jikin bango yayi da sauri ya maida kanshi kanta sannan ya zabura ya mike shima yayi bandakin,dan saura kaɗan ya makara, Tana isar da sallar tashi tayi ta koma falo ta zauna,dan ji take gaba ɗaya zaman ya ishe ta, TV ta kunna tana kallon labarai har kusan Ƙarfe tara. Jin motsi a gefen ta ne yasa ta juyo tana kallon shi,ikon Allah,shi gaba ɗaya wai kayanshi na Gonjo ne, Ya wani saka boturin riga har wuya sai kace ɗan zamin 1950, "Me kike kallo na" Ya faɗa har da ɗaga mata gira, Bata masan sanda ta fashe da dariya ba,dan wallahi abun ko kyau bai mashi ba, Kallon ta yake yana nazarin me take ma dariya "Sumi Baby me kike ma ɗariya " Nuna shi tayi da hannu"yanzun kai dan Allah ko kunyar fita a haka ba ji, Ka ganka kuwa,wannan yanda kasan wanda aka dauko daga 1950" Ta faɗa tana kara fashewa da wata dariyar. Kallon kayanshi yayi ya kalli Sumayya yanda take ta kwasan dariya kamar ta samu wawa,"amma dai kam Sumayya baki tsoron Allah,kin San kuwa yanda ƴan mata ke bina na aure su ? "A'a Jauro karka shuto min tun da safiyar nan,ai ko ƴan matan ƙauye sun waye yanzun sun san wanka" Ji yayi ranshi ya fara baci,dan haka bai kulata ba ya nemi guri kan kushin ɗin ya zauna shima,yana sauraren yanda take mai dariya, Ganin bai kula ta bane yasa tayi shiru tana kyara zama"ni fa yunwa nake ji" Gani tayi ya dauki Telephone ya danna wasu number sai kuma taji yana bada ordan abinda za'a kawo, Kyaran murya ta yi tana ɗan marairaicewa "Jauro" Ta kira sunan shi, Kin juyowa ya kulata yayi,sai ma ƙara kauda kai da yayi, "Jauro" Ta kara fadada a ɗan shagwabe, Nan ma bai juyo ba, Ɗan langwabe kai tayi "please mana ka kula ni" Juyowa yayi yana kallon ta sai dai bai ce mata komai ba, Ɗan murmushi ta sake kaɗan tana kara wani marairaicewa "dan Allah in za'a kawo abinci a kawo min mai nauyi kaji" "Da kika yi sallah kin gaishe ni? Ɗan zaro ido tayi" Lah,ai naga kana sallah ne shi yasa," "To dana fito fa? Turo baki tayi amma data tuna abinda take son roƙon shi tuni ta mai da bakin" Ai dama yanzun zan gaishe ka,shine ka tare numfashi na"saukowa tayi ta tsugunna katsa,"Ina kwana ranka ya daɗe? Gani tayi cikin sauri har yana zabura ya daga kafarshi dake a kasa ya hade da kirjin shi ya takure yana kallon ta a tsorace "Sumi? " Na'am yallabai " "Ba dai shirin kashe ni kike yi ba ko? Dago kai tayi tana mai kallon rashin fahimta, shi kuma yana mata kallon zargi da tsoro, "I know dos days is very easily to young lady like you to kill her husband shi yasa nake tambayar ki,what are you planning?me yasa da zaki gaishe ni kika tsugunna har da kirana yallabai? Bude baki tayi galala tana kallon shi,can kuma sai ta sheke da wata dariyar tana nuna shi" Wai dama Fulani na tsoron mutuwa,i can believe it,Jauro," Ƙara matsawa yayi"mata abin tsoro ne" "Kaga nifa dama so nake na tambaye ka akan ka ara min wayar ka na kira Mama,sai kuma ka mai da ni gidan da zan zauna in da zan rinka ganin mutane" Shiru yayi kamar ba zai yarda da abinda ta faɗa ba,sai kuma ya saukar da kafa yana kyara zama,tare da miko mata wayar bayan ya cire key, Murmushi tayi tana amsa, "Amma dai daga yau karki ƙara kirana da yallabai,kuma in zaki gaishe ni karki ƙara tsugunnawa har sai ranar dana yarda daki" "Kana nufin baka yarda da ni bane? Ta fada tana saka number Mama. Bai bata amsa ba ya mai da hankalin shi kan TV. Sai da tayi kira kusan sau hudu sannan aka ɗauka,ta san halin Mama tana iya ajiye wayar ma ta manta in da ta ajiye, Lokacin da taji muryar Mama tana fadin Assalamu alaimun har wani ajiyar zuciya ta sauke tana lumshe ido tamkar wacce ke gabanta haka take ji, Jin ta kara yin sallamah ne yasa ta amsa tana kiran sunan ta"Mama na" Daga inda take zaune tana iya jiyo yanda Mama ta zabura tana kiran Sunan ta"Sumayya,Sumayya ce! Ji tayi kwalla ya ɗan taru mata a ido "ni ce Mama" "Alhamdulillah Allah na gode maka,Sumayya kina ina,ina kuka je tun jiya an je gidan ku babu kowa gidan a kulle hankali na ya tashi Sumayya,ko dai ya maida ke ƙauyen su ne? Dago kai tayi ta kalleshi,suna haɗa ido ya dauke kanshi, " A'a Mama muna Matasa Hotel tare dashi, " Dafe kirji tayi"na shiga uku Sumayya Hotel kuma,da auren ku,me zai kai ku in da ake ɗiban Albarka,ina shi Jauro yake" Jin hankali ta ya tashi jin kalmar Hotel kawai da tayi yasa da sauri tace"Mama ba da wani abu bane,kawai dai ya kama mana daki ne a nan saboda yace katifar na zarnin fitsari ba zai iya kwanciya a kai ba shi yasa,amma ba wani abu bane,kuma yau ma zamu koma " "Kin tabbata dai ko? Murmushi tayi" Eh Mama,ina su Aisha? "Ta tafi makaranta,kin yi waya da yayarki ne,domin ita ma hankali ta ya tashi" "A'a amma yanzun zan kira ta" "To ku dai yi ku baro Hotel ɗin nan domin bana son zaman ku a nan,dan kar Allah ya zo saukar da matsifa ya shafe ku" "To Mama" Ta faɗa tana murmushi,daga nan sukayi sallamah,wanda yayi dai-dai da Kwankwasa kofar da akayi ya bada izinin shigowa, Wannan karon ba matar jiya ɓace,cewa yayi ta kawo abincin nan a maimakon wurin cin abinci da zata kai, Jera masu shi tayi a nan gabansu ta wuce, Kallon plate din take tana kallon shi,da Aunty Amina zata kira,amma sai ajiye wayar ta yi "ina nawa abincin? Kyara zaman shi yayi a kasa yana mata nuni da hannu,alamun gashi, Nan take ta haɗe fuska " Amma na ce maka ni ba zan ci wannan jagwagwalon ba,"ta faɗa tana nuna soyayyen ƙwai da ruwan liptom da ke cikin ƙaramin kofi wanda ko madara babu haka kuma babu Biredi. Ɗaukar cup daya yayi ya shiga kurba,"ai kin riga kin ci kudin karin safen ki tun safiyar jiya,in zaki ci wannan kaci,in kuma ba zaki kici ba is fine " Yunwa take ji,ta yaya za'ayi wannan dan abun ya ishe ta,"ni ba zan ci ba"ta faɗa tana kauda kai,yayin da idon ta ke tara hawaye. Bai kulata ba har ya kammala cin abinci shi,sannan ya dauki wayar shi data ajiye gefe, "Zan iya maki taimako ɗaya" Ya faɗa yana tsayawa a kanta, Share hawayenta ta shiga yi bata kula shi ba "In dai har zaki je motsa jiki zan iya maki ordan duk abinda kike so" "Ba naso,ba zan ci ba kuma ba zan je ba,mugu kawai" "Oh tunda haka kika ce,to ai shike nan" Ya faɗa yana bar mata ɗakin ma gabaɗaya yayi wucewar shi. Karfin kukanta ta ƙara tana jin ranta na ƙara ɓaci,wannan wani irin abu ne saboda Allah in banda ɗaukar alhaki, Ta jima tana kuka anan zaune kafin ta ji ana kwankwasa ƙofa, Kamar bazata tashi ba sai kuma ta Mike da sauri tana addu'ar akan Allah yasa abincin yasa aka kawo mata, Tana buɗe ƙofar taga wani ɗan matashin saurayi a tsaye rike da madaidaicin akwati, Cikin girmamawa ya gaida ita, A takaice ta amsa tana mashi kallon lafiya,daga ina. Turo mata akwatin yayi"gashi in ji sir Jauro wai a kawo maki ki ajiye mashi" Amsa tayi ta shiga da Akwatin tana dunguran da shi nan tsakiyar falon cikin jin haushi, Har ta zauna kuma kome ta tuna sai zuwa tayi da sauri ta buɗe akwatin wanda bata ga komai ba aciki sai kayan sawar shi,irin wanda ke bata haushi, Ɗaga rigunan tayi tana ajiye wa gefe "in dai takamarka baka son cire kuɗi,idan na sadakar da kayanka ai dole ka saka kudi ka siya wasu" Ta faɗa a fili, Gabaɗaya kayan ta kwasa cikin jin haushin mai kayan tayi waje da su, Ta jima a bakin Get kafin ta samu wani Almajiri tsoho ta bashi kyautar kayan duka, Ai kuwa ba karamin dadi da saka mata Albarka tsohon ya shiga yi ba, Harda kakkabe hannu tana komawa ciki, (Allah sarki wata ta taro Fitina ta yi kyauta da kayan Jauro) *🍂JAURO🍂* (MAI ANGUWA) Story & Writing By JIDDARH UMAR 🌟🌙🌙🌙🌙🌙🌙🌟 *🌙✨MOONLIGHT WRITER'S ASSOCIATION🌙✨* https://m.facebook.com/Moonlight-writers-association-109698351308376/ *'''We are the moonlight writers we shine all over the world.''🌍'* ✍️✍️ بِسم الله الرحمن الرحيم ~~~~~~~💞💞~~~~~~~ *Ban yarda wani ko wata su saka min littafi a shafin su ko su mai da min littafi Audio ba tare da izini na ba* *35* *Wannan littafin nawa mai suna a sama na mai da shi na kuɗi,tare da Yar Tsanar Zinare,wanda yake son guda ɗaya dari uku 300,guda biyu 500 dari biyar, Hauwa Umar,Zenith Bank,2284905309,sai shaidar biyi ta wannan number 08141644865* Komawa tayi ta kwanta tana juye_juye,dan lokaci ana niman ƙarfe sha-biyu na rana ne, Ganin babu sarki sai Allah ne yasa ta tashi ta jawo kofin shafin da ya gama yin sanyi ta haɗa da wannan kwan ta ci,sannan ta iya tashi ta shiga banɗaki dan ta dauro Alwallah ganin lokacin sallah ya matso,tana cikin sallah ya shigo, Taji shigowar shi dakin barcin su,sannan tana ji ya koma falo, Aƙwatin da ya gani a gefe ne ya jawo ya buɗe, gani yayi babu komai acikin shi, Mamaki ne ya kamashi,to ina kayan shi da ya saka aka kawo suke,kodai Sule aƙwati kawai ya kawo babu kaya acikin shi, Zaro wayar shi yayi daga cikin aljihu ya danna kira, Tambayar kaya naji yana yi,sai kuma naji yayi shiru alamun yana sauraran abinda ake fada,sai kuma ya sauke wayar ya tashi ya koma cikin dakin inda ya same ta a zaune tana saman darduma tana jan carbi wanda da hannu take yi. Zuwa yayi ya zauna a gabanta ya naɗe ƙafa, "Ina kaya na da ke cikin akwati da aka kawo? Ji tayi gabanta ya faɗi amma sai ta daure ta kauda kai kamar abin bai dame ta ba, Saida ta karasa tayi addu'a ta shafa sannan ta kalle shi tace" Wasu kaya kenan ? Nuni ya mata da falo "na cikin Akwati da aka kawo" "Ohh waɗannan tsunmokaran? Cikin jin haushin rainin wayonta yace" Kayan nawa ne tsunmokarai? Ya fada yana nuna kanshi, Waro ido waje tayi tana dafe kirji "kardai ka camin waɗannan kayan masu kyau ne?"Oh My God,ni da ya kawo min akwatin na duba sai gani nayi kayan sun min kama da tsumma dan haka na kwashe na ba Almajiri " Wannan karon shi kanshi zaro idon yayi cikin tsananin mamakin ta,because he can't believe cewa ta mai kyauta da kaya masu tsada haka,"kina nufin kayan nawa kika yi kyauta dashi? Turo baki tayi"Sorry ai ni ban dauka masu kyau bane shi yasa" Lumshe ido yayi yana sake wani nauyayyan ajiyar zuciya tare da busa iska ta bakin shi, "Kin min kyauta da kaya? Ya ƙara tambayar ta dan ya tabbatar, Kauda kai tayi sai kuma ta juyo" Yauwa ka mai da ni gida kaga daga nan sai ka dauko wasu kayan naka,kaga ni ma nan ba wasu kaya ne dani ba sai kala biyun daka siyo gashi hijabi ma daya ne" Bai kula ta ba sai ma mikewa tsaye da yayi yana mata kallon ƙasa_ƙasa ya juya ya zai fita, Har yakai tsakiyar dakin sai kuma ya juyo murmushi dauke a fuskar shi yace"karki damu,anjima zamu koma gida,dan ni ma nan din ya ishe ni"ya faɗa yana juyawa tare da barin ɗakin. Shiru tayi tabi bayan shi da kallo,to me yake nufi,ko dai ya shirya mata wani abin ne,da dai taga kamar zai dau zafi,sai kuma taga ya share, Karamin tsaki taja,a fili tace,ai in ba haka na maka ba da ba zaka yi tunanin mai da ni gida ba" Wata zuciya ne yace mata to idan ya shirya maki wani abin fa, Da sauri ta girgiza kai in dai wannan ne ba abinda zai iya yi" Mikewa tsaye tayi tana ninke darduma "to Allah na gode maka,bari na fara haɗa kayana kar nazo na manta wani"tana kammala haɗa kayan sai gashi ya ƙara shigowa fuskarshi dauke da fara'a," Fito muci abinci " Dan bata fuska tayi"Allah yasa ba irin wannan jagwalgwalo bane? "Ke dai fito ki gani" Tashi tayi ta biyo bayanshi,wanda tunda ta saka ƙafarta a falon hancin ta ya shiga shako mata wani daddadan ƙanshin abinci wanda tuni ya cika falon, Da sauri ta karasa in da yake zaune ya tankwashe kafa,ita ma ta zauna tana haɗiye miyau,gani irin kayan daɗin dake gaban shi, Gasasshen kifi ne kato wanda yaji kayan yaji dana kanshi a jikinshi, Sai kuma ɗayan shi kuma romon kaza ne wanda daga gani guda daya ne kai da kafa kawai aka cire, Ta ɗayan gefen kuma lafiyayyen tuwan semolina da miyan ganye ne yaji zuku_zukun nama a ciki,sai kuma kwalayen lemu har kala biyu masu matukar sanyi, Ba abin da take sai hadiyar miyau tana jin wani irin yunwa na taso mata, Duk abinda take yi yana kallon ta, "Yauwa Sumi Baby zuba yanda zai ishe kici mana,ni ma a zuba min" Babu wani dogon nazari ko tunani ta shiga zubawa jikin ta har wani dan rawa yake ɗan Allah ya gani yunwa take ji, Bata damu da ta tsaya zuba mashi ba ta shiga cin abincin ta hankali kwance,wanda hakan ya danso ya bashi mamaki,dan a tunanin shi yanda jikinta ke rawa zai ga tana cine hannu baka hannu ƙwarya,ma'ana kafin ta haɗiye na bakinta ta tura wani, Sai dai ba haka ba dan a hankali take ci tana sake murmushi tana lumshe ido, Tabe baki yayi ya dauki kofi ya tsiyaya mata lemu ya ajiye a gaban ta, Sannan shima ya zuba nashi, Har ya kammala ya koma ita yake jira kafin ta gama,dan yanda take ci a hankali zaka ɗauka ba zata ci sosai ba,amma sai gashi tana ninan tada abincin nan tas,dan kifin kam sai da ta cinye shi,kazar ne dai baci rabi, Mike ƙafa tayi tana sauke numfashi "kai Allah na gode maka,Jauro ɗan Allah ka dunga siyo irin waɗannan nan,kaga kudin da ba'a ci baya Albarka,in kai ba zaka iya ci ba ni ka dinga siya min ina ci maka Allah zai baka lada,kuma dukiyar ka zai karu" Jinjina mata kai yayi"kar ki damu ai babu damuwa,yauwa tunda kin gama tashi mu tafi" Murmushi tayi"to bari kyara in da muka ɓata " "A'a ki barshi kawai zasu kyara" "To shikenan,bari na shiga na dauko kaya na" Tana shiga ta dauko karamin ledar data saka kayanta ta fito,dan haka tare suka fito ya mika ma ma'aikata makulli sannan suka fito farfajiyar wurin in da anan suka kuma samun wata mota sabuwa a parke tana jiran su,sai dai motar in ba ta manta ba kamar ta rannan ce, Dan haka kamar ko wani lokaci shi ya buɗe mata kofa ta shiga sannan ya kulle shima ya shiga kafin Direba ya ja motar............. *🍂JAURO🍂* (MAI ANGUWA) Story & Writing By JIDDARH UMAR 🌟🌙🌙🌙🌙🌙🌙🌟 *🌙✨MOONLIGHT WRITER'S ASSOCIATION🌙✨* https://m.facebook.com/Moonlight-writers-association-109698351308376/ *'''We are the moonlight writers we shine all over the world.''🌍'* ✍️✍️ بِسم الله الرحمن الرحيم ~~~~~~~💞💞~~~~~~~ *Ban yarda wani ko wata su saka min littafi a shafin su ko su mai da min littafi Audio ba tare da izini na ba* *36* *Wannan littafin nawa mai suna a sama na mai da shi na kuɗi,tare da Yar Tsanar Zinare,wanda yake son guda ɗaya dari uku 300,guda biyu 500 dari biyar, Hauwa Umar,Zenith Bank,2284905309,sai shaidar biyi ta wannan number 08141644865* Kafin Direba yaja motar su bar harabar Hotel ɗin, Kallon shi tayi ya maida hankali yana ta faman danna waya "Jauro gida zamu tafi" Bai Dago ba ya bata amsa da "umm" Murmushi ta sake tana mai da kanta ta jinginar jikin kujerar motar tare da sake hamma tana lumshe ido, Tun tana buɗe ido tana kallon hanya kasancewar ta san aƙwai tazara zuwa gidan nasu har ta koma dai ta mai da tanka tana kallon hanya,ji take gabaɗaya jikinta kamar ba nata ba,ita dai gata nan,ita ba'a sandare ba ita ba'a sume ba,kamar dai wacce take cikin yana yi na semi unconsciousnes,haka take jinta,ganin komai take yi tamkar a marki. *BAYAN AWA UKU* A hankali take buɗe idanun ta tana lumshewa,ganin yanda hasken dakin ke kashe mata ido,kafin ta samu ta tsayar da kwayar idanun ta a kan silin ɗin dakin wanda yaji dizai da wasu irin kyal_kyali masu daukar ido, Ta jima tana kallon silin ɗin kafin ta maida idanunta ta lumshe,tunani take yi a ina take,nan ina ne,ko dai mafarki take yi, A hankali ta juya tana sauke ajiyar zuciya tare da ƙoƙarin mikewa tsaye, Sai dai sam bata jin ƙarfin jikinta,hakan yasa ta koma ta zauna,dan sai lokacin ma take kare ma babban ɗakin da take ciki kallo, Tunda take a rayuwar ta bata taba ganin haɗaɗɗen daki ba irin wannan,komai na dakin fari da Golden color ne na dakin, Dafe kirjinta tayi domin lokaci ɗaya gabanta ya yanke ya faɗi,dan nan take zuciyar ta ya raya mata cewa ai hatsari suka yi shine ta mutu,yanzun haka ƙila tana cikin Aljanna ne, Salati ta fara jikinta na wani irin rawa na tsananin tsoro,ƙara tashi tayi ta nufe in da labule ke kadawa a hankali, Duk da irin faduwa da gabanta ke yi da irin gargaɗin da zuciyar ta ke bata akan karta leka ta je ta leko ma kanta gidan wuta,amma haka dai ta daure ta rakube tana dan leken windon, Bata masan santa ta sake baki da hanci ba tana kallon yanda ƙanƙara ke saukowa daga sama,ga kuma kankara nan daskare ta ko'ina,haka kuma tana hangan wasu irin haddaun gidan sama ta ko ina ga haske ya haska garin wanda ita bata masan Safiya bane yanzun ko rana,duk bata iya banbancewa,sai kuma motoci dake wucewa wanda ko wanne ya kunna robar gaban mota irin mai share datti ne ko ruwa,to wannan ƙanƙaran dake sauka yake sharewa, Jin wani dan kara ne yasa ta leka ta wurin,nan ma wani babban mota ta gani irin wanda ko a duniya bata taba ganin irin shi ba,motar yana kwasan kankara yana zubawa a wani wuri, irin ƙanƙaran dake kwanciya a gefen titi. Jin karan buɗe ƙofa ne yasa da sauti ta juya,tana kallon wanda ya shigo,tare da fatan Allah yasa ba Mala'ika bane, Ajiyar zuciya ta sauke tana nufar in da yake tsaye shima yana kallon ta, Rike mai hannu tayi cikin tashin hankali tace "Jauro,mutuwa muka yi ne? Nan Aljanna ne?" Kuka ta fashe dashi tana fadawa jikin shi tare da zagaya hannun ta bayan shi ta rungume shi tana kwantar da kanta a kinjin shi,"I don't wanna die young,!ban sallami Mama ba,da su yaya Amina,!"kara shigewa jikinshi tayi tana cigaba da kuka,"yanzun shi kenan mun mutu kenan,? Waiyo Allah na wallahi bana son na mutu"ta faɗa tana ƙara sautin kukanta, Shiru yayi yana sauraran ta,kenan ita a tunaninta ta mutu ne yanzun, Murmushi ya sake yana jinjina kai kafin ya haɗe fuska kuma, Shafa bayanta ya shiga yi"ai wannan shi ake kira mutuwa ta riga fata Sumi Baby,dan yau kwanan mu uku kenan a kabari," "Waiyo Mama" Ta ƙara faɗa a tsorace, Ganin kukan nata na niman zarcewa ne yasa ya dago kanta ya haɗe bakin su wuri ɗaya,yana mata kyakkyawar sumba, Bakinta na cikin nashi ya dauke ta ya maida ta kan gado yana hawa saman ta, Cire bakinta tayi cikin nashi tana kauda kai, Numfashi take saukewa da sauri da sauri, hawaye na bin idonta ita ba abinda yake mata ne a gabanta ba,abu ɗaya kawai zuciyar ta ke raya mata shi ne"I don't wanna die young?I want to go back to my family " Juyo da kanta yayi"duk abinda na maki ki min,domin anan ba ama miji cin musu,in ba haka ba wuta kai tsaye za'a wurga ki"rungume ta yayi "bana son a gefa ki wuta" Jinjina kai tayi tana ƙara shigewa jikin shi tana fashewa da kuka,yayin da shi kuma yake sake murmushi ta gefe cikin tsananin jin daɗin.......... Jauro ina ka kawo ƴar mutane😳 *🍂JAURO🍂* (MAI ANGUWA) Story & Writing By JIDDARH UMAR 🌟🌙🌙🌙🌙🌙🌙🌟 *🌙✨MOONLIGHT WRITER'S ASSOCIATION🌙✨* https://m.facebook.com/Moonlight-writers-association-109698351308376/ *'''We are the moonlight writers we shine all over the world.''🌍'* ✍️✍️ بِسم الله الرحمن الرحيم ~~~~~~~💞💞~~~~~~~ *Ban yarda wani ko wata su saka min littafi a shafin su ko su mai da min littafi Audio ba tare da izini na ba* *37* *Wannan littafin nawa mai suna a sama na mai da shi na kuɗi,tare da Yar Tsanar Zinare,wanda yake son guda ɗaya dari uku 300,guda biyu 500 dari biyar, Hauwa Umar,Zenith Bank,2284905309,sai shaidar biyi ta wannan number 08141644865* Hannun shi ya kai bayan rigarta yana ƙoƙarin jan zip din rigar kasa wayar shi ta shiga ƙara babu kakkautawa, Ji yayi kamar ya share wayar kar ya ɗauka,sai dai ba dama saboda ringen din wayar ya shaida mashi mai kira, Dan haka cikin jin haushi ya sauka daga kan gadon yana ɗaukar wayar shi da ya ajiye a gefen durowa ya kara a kunne, Ta ɗayan ɓangaren aka ce"yallabai saura mintuna goma sha biyar girginmu ya tashi,dan haka ana buƙatar ku kara so kusa" A daƙile yace"ok"yana kashe wayar tare da maida shi aljihu, Iska ya busar ta baki yana kallon yanda take kwance tana matsar hayawen tunanin ta mutu ne, Girgiza kai yayi yana cije leɓe,ya rasa wannan damar,amma ba komai,hakan ba wai yana nufin ya haƙura sai tayi kukan kayan shi data sadakar, Karasa yayi inda take kwance ya dago ta"tashi mu tafi" "Ina" Ta tambaya tana wani langabewa a jikin shi, "England zamu,domin nan muna Santiago ne" Baki ta buɗe"ina ne kuma haka" Mikewa yayi da ita"mu je ki gani dan jirgin mu ya kusa tashi" Daukar wani katon rigar sanyi yayi ya taimaka mata ta saka,sannan ta maida karamin hijabi a sama, Kallon shi tayi"ya aka yi na zo nan? Yana saka nashi kayan sanyin kai tsaye yace"abu na zuba maki a lemun kwalin da kika sha na saka ki karamin suma" Cikin mamakin shi ta zaro ido"me ka saka min? Yanzun kai Jauro ko kunya baka ji ba kake faɗa min" "Kin ga mu tafi kafin mu rasa jirgi dan ban shirya ƙara kwana a garin nan ba" Bin bayanshi tayi tana mamakin shi, Abin bai ƙara bata mamaki sai da taga a irin duniyar ƙanƙaran da take,dan fari ne mai azabar sanyi, Duk da hiter na zafi dake cikin motar da zai kai su Airport hakan bai hana su jin sanyi ba, Ganin yanda take yi ne yasa ya dan jawota jikin shi da shirin rungume ta ko zata samu dumi, Amma sai ture mai hannu tayi cikin jin haushi abinda ya mata Dazu bayan ya san ba lahira suke ba, Babban filin jirgin garin aka kai su wanda bai da wani nisa da inda suke, Tana biye dashi har aka kammala komai kafin a basu izinin shiga jirgi, Sai lokacin ta sake baki tana kallon yanda tsarin jirgin yake,yanzun ta yaya za'ayi wannan abun ya iya tashi yashi gashi ƙato sannan duk suna ciki, Rike mai hannu tayi tana shagwabe fuska "Jauro" "Umm" "Ni dai ba zan shiga wannan jingin ba,kar yazo ya yarda mu,ta yaya zai iya tashi" Kallon ta yayi,shi bai ga kauyancinta ba tunda shima irin haka ta taba faruwa dashi, Dafa hannun nata yayi da ɗayan hannun shi"karki damu akwai wadanda ke kula da shi a ciki da kuwa can,kin ga wancan ginin"ya nuna mata wani babban bene mai tsayi"to anan Controler jirgin suke " Kara rike shi tayi"ni dai tsoro nake ji" Jinjina kai yayi,sai kace ba dazu ta gama ture mai hannu ba, Saka hannun shi yayi cikin nata ya rike gam "idan muna shiga ki dinga yin Addu'a" Miyau ta hadiye tana jinjina mashi kai, sannan suka shiga jirgin yayin da addu'a ke bakin ko wannen su, Shi ya saka mata belet na kujera, Tana rungume da hannun shi a jinjnta har jingin ya daga sama dasu,. Tafiyar Awa biyu da rabi ne ya kawo su England,in da anan ma wani ne yazo ya dauke su a mota zuwa wani gida,a maimakon Hotel, Gidan madaidaici ne mai dauke da babban falo da daki biyu sai kicin da wurin shan iska, Yana rike da ƙaramin jakkan su har cikin dakin kafin ya ajiye ya juyo ya kalle ta"ni zan fita ba zan samu dawowa da wuri ba,za'a kawo maki abinci ki ci,sannan ki kwanta kin ga dare yayi anan,sannan ki rufe da bargo sosai " Da sauri ta juyo tana girgiza kai "A'a ni dai ba zan zauna ba,sai dai kaje dani,ni tsoro nake ji" Jawo ta gaban shi yayi ya subaceta a goshi,"babu abinda zai same ki saboda nan akwai tsaro sosai,"wayar shi ya ciro a Aljihu ya danna wata number "karɓi wannan wayar zamu yi waya dake idan na tafi,kuma kina iya kiran gida ku gaisa da su mama" Amsa tayi ta koma bakin gado tana zama"ƙarfe nawa zaka dawo? Kallon Agogo yayi wanda ke nuna ƙarfe takwas na dare,ƙila zuwa goma" Shikenan sai ka dawo" Ba karamin dadi yaji ba da wannan addu'ar nata,domin shine addu'a na farko da ta fara mashi tunda yake da ita,"Amin"ya ce fuskar shi dauke da murmushi, sannan ya fita, Bai jima da fita ba aka kawo mata abinci kamar yanda ya faɗa,abinda ya mata matukar daɗi shine ganin soyayyar dankalin turawa da kuma kyau ba laifi abincin da ɗan yawa sai fruit salad wanda yaji ya'yan itatuwa, Sai da ta ci ta ƙoshin kafin ta kwanta, Kafin ma ya dawo ta yi barci, Dan haka shima kwanciya yayi a gefen ta yayi barci shi hankali kwance ba tare da ya matsa ko kusa da ita ba, Washegari da safe ma koda ta tashi tuni har ya fita,sai dai ya rubuta mata wasika dan karamin ya ajiye mata,ko da ta tashi ta ganshi,duk da ba wata jituwa ɓace a tsakanin su amma bata ji daɗi ba dan ko ba komai dashi ta saba, A ranar haka dai tayini daga kallo sai Games da take ta bugawa a wayar daya bar mata, Ranar ma bai dawo ba sai kusan takwas na dare lokacin ma bata jima da cin abinci ba, Zama yayi kusa da ita,amma bata ce mashi komai ba,sai ci gaba da game dinta da tayi, "Wai Sumi Baby baki ga na dawo bane" Kallon shi tayi"naga ka dawo" "To shi ne ko dan zuwa ki rungume ni baki yi ba,na dai san kina kallon fina-finan turawa yanda suke tarban mazajen su in sun dawo aiki,sufa har kiss za'a maka,dan Allah ki dinga koyi dasu" Wani irin kallo take mai tana ya mutse fuska"Allah kiyaye na maka kiss " Zaro ido yayi"yanzun har kin manta irin sambatun da kike tayi jiya a Aljanna," Bata fuska tayi, "Bari na tuna maki,haka kike yi,Jauro I don't wannan die young,sannan kika hau tonde min baki kamar zaki cinye min baƙi,kinsan ni ma dana fara sake maki zafafa,sai kika shiga nishi kina faɗin wash,waiyo daɗi,kina wani bankaromin kirji kina cewa in taba nan" Ganin yanda ta sake baki tana kallon shi cikin mamaki ne yasa yace"Umm karki damu ai ni da yake ba ɗan iska bane shi yasa ban taba ba,duk da naso na taba tunda sunata tsole min ido,sai dai da ki sani nan gaba kina cewa taɓa taɓawa zan yi " Wani irin ihu tayi tare da tashi zata Hai kanshi,ai kuwa da gudu ya tashi yana dariyar mugunta,nan da suka shiga zagayen falon tana binshi tana kuka"ni yaushe nayi haka,ni sharri kake min" Juyowa yayi yana mata gwalo tare da turo mata kirjin shi yana nuna mata irin yanda take yi "haka fa kike turo shi,kin ga dama dai na ɓoye maki ne amma har da cewa kike Jauro kami" Tsayawa tana zaro ido da buɗe baki"kamin me? "Abun" "Abun? Me abun? Kafaɗa ya daga " To ni ma shine nake son na tambaye ki,me abun,ko dai kina nufin,laaaaaa,wallahi ni ba dan iska bane" "Kanen nice yar iska? Ta faɗa tana takowa inda yake yayin dashi kuma yake matsawa baya yana mata dariya, " Kaji tsoron Allah Jauro,ka tuna me karya ɗan wuta ne" "Ai naga alama ke kina tsoron Allah" Da gudu ta ƙara binshi cikin tsananin jin haushin sharrin da yake mata,ita duk yaushe tace mashi haka, Ai kuwa a maimakon taga ya juya yana gudu,sai gani tayi ya nufi to shima da gudu,kokafin ta tsaya tayi tunanin juyawa har taji yayi sama da ita ya rungume ta tare da haɗe bakinsu wuri guda yana juyi da ita yana kissing ɗinta,yanda kasan zai ciye mata bakin,kafin kuma taji ya direta kan kushin duk da haka bakin su na manne, Kokarin ture shi take yi sai dai ya manne mata yanda kasan wanda aka haɗa magnet, Tunda take dashi bata taba kai tsaye ya kai hannun shi kan kirjin ta ba sai yanzun data tsince hannun shi saman nipple ɗin ta yana murza, Ture shi tayi da karfi tana tashi zaune,"ai kai ne ɗan iskan" Shima matsawa gefe yayi yana sauke numfashi"ai dai da matata nayi iskanci ba da matar wani ba" Kin bashi amsa tayi sai ma goge bakinta data shiga yi tana hararanshi, Mikewa tsaye yayi "duk ki gama da kanki zaki ni ne ni" Nan ma shiru ta mai dan ba karamin haushi yake bata ba,ta lura ko zasu kwana a haka shi ba gajiya da magana zai yi ba, Har ya fara tafiya sai kuma ya juyo"akwai kankana a kicin dan Allah ki nika min shi sai ki kawomin ruwan"ya faɗa yana shigewar ɗaki Tashi tayi ta shiga kicin din ta buɗe firig ta dauko,sai da ta cire yayan sannan ta hau nikawa, Minti biyu ta kashe injin,tana shirin juyewa a kofin ne ya shigo, Kallon yayan kankanan dake gefe yayi,bai ce mata komai ba ya amsa wanda ta zuba mai a kofi ya kasa kai ya shanye, "Ke ba zaki sha bane? " Yanzun zan nika" Kokarin cire yayan kankanan tayi"A'a karki cire yayan,ki nika da shi sai ki saka madaran ruwa yana wanke mara sosai,duk wani dattin dake mara sai ya fita" Kallon shi tayi "da gaske? " Sosai ma"ya faɗa yana barin kicin din, Ai kuwa juye kankanan tayi ta dibo yayan nashi data cire ta haɗa ta nika duka,tana gamawa ta dauko madaran ruwa gwangwani daya ta juye ta ƙafa kai ta shanye, Daga inda yake labe yana kallon ta wani dariya ya saka a zuciyar shi a fili kuwa har da ɗan tsallen murna,domin ya san irin muguntar daya mata wanda yau dai dole ta nime shi da kanta, Domin ya'yan kankana ba karamin ta da sha'awa suke yi ba,ba ma ɗan kaɗan ba,balle aje ga kan madara wanda shi kanshi kadai idan mutum ya sha yana tada sha'awa,to balle ita data haɗa duka biyu, Ganin tana kokarin fitowa ne yasa da sauri ya koma kan kushin ya zauna tamkar dama kallo yake yi, Ita ko bata ce mashi komai ba ta shige ɗaki domin tayi shirin kwanciya ta kwanta.......... *🍂JAURO🍂* (MAI ANGUWA) Story & Writing By JIDDARH UMAR 🌟🌙🌙🌙🌙🌙🌙🌟 *🌙✨MOONLIGHT WRITER'S ASSOCIATION🌙✨* https://m.facebook.com/Moonlight-writers-association-109698351308376/ *'''We are the moonlight writers we shine all over the world.''🌍'* ✍️✍️ بِسم الله الرحمن الرحيم ~~~~~~~💞💞~~~~~~~ *Ban yarda wani ko wata su saka min littafi a shafin su ko su mai da min littafi Audio ba tare da izini na ba* *38* *Wannan littafin nawa mai suna a sama na mai da shi na kuɗi,tare da Yar Tsanar Zinare,wanda yake son guda ɗaya dari uku 300,guda biyu 500 dari biyar, Hauwa Umar,Zenith Bank,2284905309,sai shaidar biyi ta wannan number 08141644865* Tana gama canja kaya ta kwanta tare da jawo bargo ta rufe gabaɗaya jikinta dashi,bata wani jima ba barci mai daɗi ya dauke ta, Shima tashi yayi ya shigo dakin fuskanshi dauke da murmushi yana kallon ta, Hawa kan gadon yayi ya kwanta,yana fuskantar ta,ta yanda zata iya shakar numfashin shi, A haka barcin ya dauke shi shima, Ko barcin awa daya bata yi ba ta farka saboda wani irin kullewa da maranta yayi,ga kuma tsigan jikinta da taji yana tashi, Shiru ta yi tayi likimo tana kallon shi yanda yake barcin shi hankali kwance, Ita gata ma ko numfashin shi da take shaka ji take jikinta na mata wani irin zir_zir haka take ji,gabaɗaya tama rasa me ke mata daɗi, Wani irin sha'awa ce taji ya taso mata nashi wanda ta rasa ta menene, Abu ɗaya kawai ta sani shine haka kawai taji tana son ta taɓa shi, Hannun ta takai a hankali kan fuskar shi ta shafa, Sai kuma ta ɗaga hannun da sauri tamkar wacce akaiwa Shock, Ajiyar zuciya ta sauke tana duya mashi baya,dan sam bata son ta taba shi kamar yanda zuciyar ta ke raya mata, Ji tayi numfashi mai matukar dumi yana sauka a dokin wuyar ta,wanda hakan ne yasa ta maida ido ta lumshe da ƙarfi,dan zuwa lokacin ji take yi maranta kamar ana kirtan ta,saboda yanda wani abu yazo ya dunƙule a wurin,ga kuma jikinta dake mata wani irin kaikayi da mugum muradin wani abu wanda bata San ko me bane, Ƙara juyowa tayi,tana zuba masa idanun ta da suka fara sauya kala saboda azaba, Ji take kamar ta jawo shi jikin ta,ko ta sumbace shi, Abinda take jin tana son yi kenen, Numfashi kawai take saki yayin da gaban ta ce sananta faɗuwa a lokacin data dukar da kai tana ƙoƙarin daura bakin ta saman nashj, Wata zuciya ce ta kwabeta akan kar ta aikata kuskure,dan idan ya motsa me zata ce mai,kai ina ba girmanta bane, Shi kuma ganin tana ƙoƙarin ɗaga kanta ne yasa ya shiga addu'a a zuciyar shi akan Allah yasa karta fasa,domin tun shafar farko data ma fuskarshi ya farka, Ganin da gaske dai janye fuskar nata zata yi yasa da sauri ya riƙo fuskarta da hannayen shi biyu ya haɗe bakinsu wuri ɗaya, Cikin natsuwa ya shiga sumbatarta ta yanda zata ji daɗi kuma abin ya kara taso mata, Ƙoƙarin cire bakinta cikin nashi take yi,sai dai ji take tamkar wacce ake tunzurawa dan haka bata masan sanda ta zagaye hannayenta a wuyan shi ba ta shiga mai da mai da martani cikin nata kwarewar, Tofa su Jauro an samu yanda ake so,dan haka kara rungume ta yayi sosai a jikin shi, Ji yayi ta kai hannun ta tana ɓalle botiran rigarshi na barci,wanda hakan ne yasa ya dakata da abinda yake mata, Ya gado kai yana kallon ta, Ita ma jin ya tsaya ne yasa ta dago kai tana kallon shi da shanyayyun idanun ta, Lumshe idanun ta tayi tana ƙara buɗe su a kanshi,kafin ta buɗe baki da kyar ta iya cewa"mara ta na ciyo,mutuwa zan yi" Ta faɗa tana kwantar da kanta a kan kirjin shi, Yayin da ya tsinci hannun ta daya yana wayo a saman kirjin shi tana zagaye kan kirjin shi dashi, Jin tana kokarin daurashi akan layi ne yasa ya damki hannun ta,yana mirgina ta gefen shi ya zama na tayi filo da hannun shi, "Faɗa min me kike so," Girgiza kai tayi tana jin hawaye na taruwa a idanun ta"ban sani ba" Shiru yayi yana nazarin ta,shi da sam bai ɗauka cewa haɗin da yasa tayi zai mata reacting haka ba,daga dukkan alamu to tana da karfin sha'awa, Yanzun ya san kome zai mata baza ta musa mashi ba, *🍂JAURO🍂* (MAI ANGUWA) Story & Writing By JIDDARH UMAR 🌟🌙🌙🌙🌙🌙🌙🌟 *🌙✨MOONLIGHT WRITER'S ASSOCIATION🌙✨* https://m.facebook.com/Moonlight-writers-association-109698351308376/ *'''We are the moonlight writers we shine all over the world.''🌍'* ✍️✍️ بِسم الله الرحمن الرحيم ~~~~~~~💞💞~~~~~~~ *Ban yarda wani ko wata su saka min littafi a shafin su ko su mai da min littafi Audio ba tare da izini na ba* *39* *Wannan littafin nawa mai suna a sama na mai da shi na kuɗi,tare da Yar Tsanar Zinare,wanda yake son guda ɗaya dari uku 300,guda biyu 500 dari biyar, Hauwa Umar,Zenith Bank,2284905309,sai shaidar biyi ta wannan number 08141644865* Jawo ta jikin shi yayi ya rungume ta,ya shiga shafa bayanta a hankali tamkar mai lallashin yaro, Ita baisan wannan shafar bayan da yake mata ji take tamkar yana ƙara taso mata da wata fitinar ɓace, Hannunta tashiga turawa cikin rigar shi,sai dai da mamakinta sai gani tayi yana zame mata hannu,alamun dai baya son taɓa shi da take yi, Haushi ya bata dan haka mirginawa tayi gefe ta juya mashi baya,yayin data shiga sharan hawaye cikin jin haushin abinda ya mata,domin zuwa yanzun kam ta fahinci abinda take ji, Tun tana yi a hankali har shesshekar kukanta ya fara fitowa,ji take kamar zata mutu, Gaskiya ba zata iya ba,juyowa tayi suna fuskantar juna ita dashi, Gani tayi idanun shi sun yi ja sosai sun canja kala,duk da irin halin da take ciki hakan bai hana ta tsura mashi ido ba,tamkar yanda shima bai cire idanun shi a nata ba, Idan dai har ba rashin fahimta tayi ba,tamkar tsananin damuwa da ɓacin rai ta hango a idanun shi,sai kuma wani maiko da idanun ke yi,tamkar wanda hawaye ya kwantawa,kai anya ma ba hawaye bane, Jin yanda maranta ya kara tsikaran ta ne yasa ta lumshe ido tana cizan labbanta, Hannun shi ta danko da ƙarfi "Jauro please! Lumshe ido yayi sai kuma ya kara buɗesu a kanta. Wasu hawayen ne suka zubo mata"please Jauro help me,ba zan iya ba,mara na!,dama kace ni zan nime ka,to gashi na nime ka,dan Allah ka taimaka min Jauro" Ta faɗa tama rungume shi jiminta tare da hada bakin ta da nashi tana tsotso. Rungume ta yayi shima yana cigaba da sunbatar ta kafin ya gangaro ya shiga sumbatar wuyanta, Hannu tasa tana shirin cire mashi riga, Sai ji tayi ya tureta gefe da sauri yana mikewa tsaye,jikin shi har rawa yake,gashi kuma fuskar shi tayi jawur, Hannu yasa ya dafe kanshi,jin yanda ta fashe da kuka, Da sauri ya juya ya shige ban daki tare da bugo kofa da ƙarfi, Kunna ma kanshi shawa yayi,da karfi ruwan ya shiga sauko mashi,jin gina yayi da bango ya lumshe ido,yana jin yanda zuciyar shi ke tafasa jikin shi na fitar da wani irin tururi tamkar wanda ruwan zafi ya zubar ba, A kai akai ya shiga sauke nunfashi yana jin yanda kukanta ke tashi, Ya dau sayin lokaci a ban dakin kafin ya fito daure da towel a kugunshi, Kallon inda take kwance yayi,ta dunkule wuri ɗaya ta juya ma kofa baya, Inda ya ajiye kayansa ya nufa ya canja wasu kayan barcin,sannan ya fita, Bai wani jima ba sai gashi ya kara shigowa hannun shi rike da kofi madaidaici, Tsayawa yayi a gefenta,"tashi kisha wannan zaki samu sauki" Ya maimaita kusan sau uku amma yaji shiru ba amsa, Kiran sunan ta yayi,nan ma shiru ba amsa, Hannu yakai zai taɓa ta,sai kuma ya janye hannun shi da sauri, Gabaɗaya ya rasa yanda zai yi da ita"ba dan ni ba,ba dan na isa ba,sai dan darajan aure dake tsakani na dake,dan Allah ki tashi" Sai da ta ƙara ɗiban wasu mintuna kafin kuma ta tashi ta zauna, Idanun ta sunyi jawur sun kunbura, Miƙa mata kofin yayi,yana tsugunnawa a gaban ta,"kisha wannan zai taimaka maki" "Bazan sha ba," "Ba dan ni ba sai dan Allah" Ya faɗa yana kallon yanda take lumshe ido alamun har yanzun tana cikin wannan yanayin. Karba tayi ta rike a hannun ta tana jin yanda dumin kofin ke ratsa ta, Kallon shi tayi,har yanzun fuskar shi a dame yake tamkar yanda jan da fatar tayi bai washe ba, Duk yabi ya wani marairaice, A hankali ta shiga kurɓa tana dan ya mutse fuska,ga dai shi a ido kamar Coffee sai dai dandanun ba na coffe bane, Baida yawa dan kurba huɗu ta mai ya kare, Ƙoƙarin komawa tayi kan gado ta kwanta da sauri ya dakatar da ita"karki kwanta" Ko kallon shi bata yi ba,ta haye kan gado tayi kwanciyar ta, Hmm ji tayi cikinta gaba ɗaya ya hautsine yanda kasan wacce ta ci mai ko,kafin kace me,taji amai na ƙoƙarin zubo mata,da mugun sauri tayi banɗaki wanda kafin ma ta karasa shiga cikin bayin har ya kucce mata, Dan haka nan ta tsugunna ta shiga kwara amai kamar zata amayar da hanjin cikinta, Yana tsaye a gefen ta da ruwa a buta yana jera mata sannu, Sai dai har ta gama bai taɓa ta ba,sai ruwa daya zuba mata a hannun ta wanke baki sannan ta tashi ta koma kan gado ta kwanta tana maida nunfashi, Yayin da take jin wani irin haushin shi a zuciyar ta,na abinda ya mata, Wani tunani ne ya faɗo mata a zuciyar ta wanda yasa da sauri ta juya bakin kofar bayin tana kallon shi yanda yake wanke aman da tayi,ɗan waro idanun ta tayi"ba dai mata maza bane,a'a ba mata maza ba,yama ake kiran irin su,uhhhh,oh God,irin mazan da ba su da karfin mazan taka,,duk yanda akayi haka yake,Ashe dama duk abinda yake mata burga ne babu abinda zai iya,ai kuwa ya shiga uku,shine harda sakata wanke kashin kaji"ganin yana ƙoƙari fitowa ne yasa da sauri ta kara juyawa tana lumshe ido. Tana jin ya jawo bargo a durowa ya daura saman kushin,kafin ya dawo in da take kwance ya leka yana kiran sunan ta"Sumy Baby kin yi barci ne"jin shiru yasa ya juya ya koma kan kushin ya kwanta, Ya jima idanun shi biyu ya zurfafa cikin tunani har bai san sanda barci barawo ya wuce dashi ba, Tamkar yanda ya kasance a ta bangaren ta. Washegari da asuba yana tashi ya tada ita,shi ya fara yin Alwallah kafin ta shiga tayi wanka ta dauro Alwallah ita ma,tana jin jikin ta sayau babu nauyi, Koda ta fito yana zaune yana jiran ta, "Kiyi sauri ki shirya lokacin sallah na tafiya" Juyowa tayi gabaɗaya tana kallon shi"ni kake jira" "Umm" Murmushi ta sake"bazanbi sallah wanda bai amsa sunan shi namiji ba," Kallon mamaki yake mata "me kike nufu"? " Kawai kayi sallar ka nima zan yi nawa" Bai ce mata komai ba ya tashi yayi sallah shi dan ya lura sawa zata yi ya makara, Ko da ya idar ya daɗe yana jan carbi har gari yayi haske sosai sannan ya tashi ya shiga wanka ya shirya ya fita. Ba ita ta tashi barci ba sai kusan goma na safe, Wanke bakin ta tayi ta fito falo in da ta samu lafiyayyen kunun gyada da kosai mai zafi acikin kula karama, Ko ina ya samo shi ohho,ita sai ya mata daɗi sosai, Sai dai kunun ba wani yawa ne da shi ba. Ko kammalawa bata yi ba sai gashi ya shigo rike da babban leda a hannun shi, Zama yayi kusan da ita"hala baki ji ina amsa sallamah? Jinjina kai tayi tana jin daɗin kosan wanda akwai nama a ciki,"gaskiya kosan nan yana da daɗi " "Ga kaya nan ki shirya anjima zamu fita zuwa sha ɗaya" "Babu inda zanje dan ba zan fita da wanda bai amsa sunan shi namiji ba" Shiru yayi yana kallon,harya ya buɗe baƙi zai yi magana,sai kuma ya sauke ajiyar zuciya yana murmushi,"ki dai shirya domin yau za'a bani takardar shaida zama na young professor a matsayi na na wanda bai gama cika shekara talatin ba,idan mun dawo zamu shiga kasuwa dan gobe insha Allah zamu koma" "Ai kuwa gara mu koma ka bidar ma kanka magani" Bai bata amsa ba ya tashi ya shige ɗaki,dan yasan idan da ace tasan menene matsar da zama zatayi ta dinga rusa ihu tana niman taimako, Amma babu komai koma menene ke shirin tun karo rayuwar su Allah zai sa sufi karfin shi,amma maganar gaskiya jiya ba karamin tashi hankalin shi yayi ba da daddare......... *🍂JAURO🍂* (MAI ANGUWA) Story & Writing By JIDDARH UMAR 🌟🌙🌙🌙🌙🌙🌙🌟 *🌙✨MOONLIGHT WRITER'S ASSOCIATION🌙✨* https://m.facebook.com/Moonlight-writers-association-109698351308376/ *'''We are the moonlight writers we shine all over the world.''🌍'* ✍️✍️ بِسم الله الرحمن الرحيم ~~~~~~~💞💞~~~~~~~ *Ban yarda wani ko wata su saka min littafi a shafin su ko su mai da min littafi Audio ba tare da izini na ba* *40* *Wannan littafin nawa mai suna a sama na mai da shi na kuɗi,tare da Yar Tsanar Zinare,wanda yake son guda ɗaya dari uku 300,guda biyu 500 dari biyar, Hauwa Umar,Zenith Bank,2284905309,sai shaidar biyi ta wannan number 08141644865* Yana ajiye ledar komawa yayi ya zauna kan kushin yayi shiru,idanun shi a lumshe,gabaɗaya ya rasa me ke mai daɗi,ya kuma rasa tunanin me ya kamata yayi, Dazu moha da suka yi waya yake sanar dashi cewar Matar Baffa sanda an sake ta,wai da safe maza sun fito zasu sallah masallaci suka ganta a daure a iccen kofar gida,gaba ɗaya ta rame ta fita hankalin ta,yanzun haka tana asibiti a kwance, Su kuma ƴan kidnapping din sun ce sai an cika masu kuɗin su sannan zasu sako Baffa sanda. Jin motsi ne yasa ya buɗe ido yana kallon in da take tsaye, Ba tare da wata shakka ko damuwa ba ta cire zoguwar rigar data saka dazu,ya rage daga ita sai bireziya da dogon wanda a jikin ta, Tsabaragen mugunta irin na Sumayya sai da ta juyo suna fuskantar juna ita dashi sai dai ko kadan bata kalli inda yake ba,ta sa hannu ta ballle maɓallan bireziyar ta, Lumshe idanunshi yayi da karfi yana buɗewa,ji yayi maƙoshin shi ya bushe,da kyar ya tattato miyon bakinshi ya haɗiye "Sun.... Sumy Baby me haka kike yi" Juyowa tayi da kyau cikin salon iskanci ta shiga kaɗa kirji,wadanda suke a tsaye suka kallon shi "name fa? Kauda kai yayi yana kyara zama da kyau dan ji yake tamkar ana jawoshi ƙasa daga inda yake zaune" Ki suturta jikin ki mana, baƙi ganin akwai mutum a dakin? Kalle_kalle ta fara "ai ni banga wani mutum aciki ba face mijina" Sai kuma ta tabe baki tana wani shagwabe fuska "ko da yake mijin ma bashi da amfani tunda jiya har tayi akai masa amma ya gaza tabuka komai" Ta faɗa tana saka wata bireziyar data ɗauko,ta jawo leda kayan daya bata ta fito dashi, Ita karan kanta ta yaba domin jallabiya ce doguwa ruwan madara ta haɗu sosai,dan ba karamin shan duwatsu yayi ba, Tana sakawa kuwa sai gashi ya zauna a jikinta tsaf yanda ake so, shi baiyi yawa sosai ba shi bai matse ba,sannan ta nada madaidaicin gyalan a kanta, "Anaki tunanin kenan ko?humm,Gara dai ki dinga suturtawa dan baki san sanda Damo zai waiwaye harawa ba" "Koda ma ya waiwaye harawar sai dai ya tumurmusa baki,amma fa ada kenan,balle yanzun da ko yaje babu abinda zai iya yi balle haryaci harawar" Daga inda yake zaune yana kallon ta ya tsince kanshi da sakin murmushi,shi mutum ne da sam baya ɓoye abinda ke ranshi ko ya kauda kai"kin yi kyau sosai Sumy Baby,yanda kikasan kin haɗa jini dasu"ya faɗa yana basar da maganar ta dan shi san baya ganin laifin ta, Ba tare data juyo ba tace"tubarakallah,masha Allah,karka cinyeni" Mikewa yayi tsaye yana murmushi,ya zame rigar dake jikin shi,yana ƙoƙarin cire wando ne ta juyo ta kalle shi, "Me kake yi haka? " Kaya zan cire" Zama tayi bakin gado tana kallon shi ba tare data bashi amsa ba. Ba tare da tayi tunanin zai iya ba sai gani tayi kawai ya zame dogon wandon dake jikin shi yana ƙoƙarin cire gajerin, Zabura tayi ta mike "lallai baka da kunya yanzun kai haka kawai sai ka tube a gaba ba" "Ba laifi bane indan miji ya tube a gaban matar shi kamar yanda matar ta tube a gaban shi," Turo baki tayi ta mike tana barin dakin tare da fadin "ni dai ba yar iska bace" Cire kayan jikinshi yayi ya canja zuwa faran shadda kar da hula,sai takalmi, Tunda take dashi wannan ne karo na farko a rayuwar ta dashi data taɓa ganin shi da kayan daya mai kyau kuma ya zauna a jikin shi, "Tubarakallah masha Allah,hakan ya kamata ki faɗa" Kauda kai tayi daga zuba mai idon da tayi"ai dai ko kyau ba kayi ba" Gwalo ya mata "na dai kamaki kina kallon na ba," Yamutse fuska tayi tana mikewa tsaye"banga abin kallo ba anan" Bude mata kofa yayi suka fito ya maida kofar ya kulle, A hankali suke takawa har suka iso Bus Stop,na layin inda suka shiga, Ita dai sai kalle kalle take yi har Bus din ya tsaya,suka sauka,nan ma basuyi wani tafiya mai nisa ba suka iso wani babban ɗakin taro wanda yake cike da mutane, Domin su komai akan lokaci suke yi, Suna shigowa wani Bature ne ya taso da sauri yazo in da suke,gani tayi sun rungume juna su,sai kuma taji nan take ya juya harshe cikin kwarewa yake magana da Turanci, Abinda bata taba zata ba,har yanzu ba zata iya cewa waye asalin mijin da take aure ba,ta dai san sunan shi,amma wasu abubuwa nashi baza ta iya kararwa ba, Wani kujera na musamman taga an nuna masu inda zasu zauna, Suna zaune sai ji tayi an kira sunan shi,sai kuma taga mutane sun shiga tafa mashi, Ita kallon su kawai take tamkar wata wawuya domin in tace tana fahimtar duka abinda suke fada tama Allah ƙarya,sai dai abinda ba'a rasa ba, Taga kuma wani dattijon Bature ya bashi wasu takardu da kuma wani abu kamar a Glass anyi rubutu aciki,sai ɗaukarsu hotuna ake yi ta ko ina, Daga karshe kuma JAURO yayi godeya da bayani sosai a harshen Turanci, Ji tayi jikinta yayi sanyi,ta raina kanta,kalli irin hadaddun matar dake ta zuwa suna tayashi murna,basu damu da kalar shi ba ko shigar shi, Shi yasa bai da kyau ka kyamace mutum saboda bai da wani abu,domin ta iya yuwa kai ma akwai abinda baka dashi amma shi Allah ya bashi, Gani tayi ya mata alama da hannu alamun ta zo, Tasowa tayi tazo inda yake tsaye tare da wadanda aka basu shaida tare,hotuna sosai aka shiga dauka,sannan yana ta nuna ma abokin shi ita amatsayin mata, Dole dai tayi masu yake,sannan ta gaisa dasu da ɗan Turanci da take ji. Sun dan jima sosai a wurin kafin su fito, Tayi tunanin gida zasu koma,sai dai kasuwar garin taga sun nufa dashi inda anan tayi kallon abuwa iri-iri, Kallon ta yayi"Albarkacin farin cikin da nake ciki a wannan ranar,ki ɗauka duk abinda ya maki zan biya kuɗin " Zaro ido tayi "kana nufin da gaske? " In baki so mu tafi" Tsabar farin ciki yasa bata san sanda tayi tsalle ta rungume shi ba"waiyo Jauro na gode " Gani tayi da sauri ya cire ta a jikin shi yana matsawa baya kaɗan, "ba sai kin taɓa ni ba " Dakatawa tayi tana kallon shi har ya shiga fiffita da hannun shi kamar mai jin zafi, "Me yasa baka son in taɓa ka" Da sauri ya sake murmushi "is that necessary? Sake fuska tayi tana jawo wani doguwar riga " Wow,gaskiya wannan zai ma Mama kyau sosai, Ba karamin yawo suka yi ba,ta zaɓar ma Aisha da Aunty Amina kaya,harma da Salma, Har zasu wuce ta hango shagon da ake sai da kayan maza,"Jauro muje shan shagon " Kallon kwalayen dake hannun shi yayi"kinga lokacin sallah har tayi baki gama ba" "Ɗan Allah mana,wannan ne na karshe" Tsaki yayi,yasan dai bai wuce Babanta zata daukar ma tsaraba,suna shiga ya samu wuri ya zauna,"kiyi ki gama mu tafi" "Ok " Ta fada tana ƙarama shiga cikin shagon sosai, Bai san kalan kayan data siya ba sai da ya je biyan kuɗi yaji kudi masu yawa ga kuma kwalaye sun kai biyar,"Sumy Baby gaskiya ki rage kayan nan kudi yayi yawa" Bata fuska tayi "kaifa kace na dauki duk abinda nake so,zaka biya,me yasa zaka canja maganarka yanzun? Kauda kai yayi yana sauke numfashi,tare da basu umurnin su cire kuɗin. Haka suka dawo gida da kaya niki_niki,haka ta dinga cirowa tana dubawa,tana kuma ninkewa tana jerawa a babban jakkan da suka siya. __________Nigeria. Dariya take ta fama tuntsira yanda kasan wacce ta ga wawan zama, Matar dake gefen ta ne tace"wai daga magana ke kuma sai ki hau dariya kamar kin samu shashashai " Tsagaitawa tayi"ke kuwa ya za'ayi ba zan yi dariya ba,kin taba ganin shashashar uwa da batasan in da ƴar ta ke aure ba," "Naji tace a Tunga aka kai ta,ko ba haka kika ce ba Maman Aisha" Matar ta faɗa tana kallon inda Mama ke zaune. "Haka ne Goggon su" "Kensan ni ban samu naje bikin bane shi yasa nake son naje naga gidan a matsayina na kanwar mahaifinta" "Ai in faɗa maki gaskiya tun randa aka kai ta washe gari da aka je budan kai babu kowa a gidan har yau ina faɗa ba a san in da yayi da ita ba,ko da yake na tabbatar da yanzun haka suna ƙauye" Dafe kirji tayi tana salati "ba dai ƙauye Sumayya zata zauna ba" "Kamata yayi goggon su ki ce,yanzun a ƙauye Sumayya ke zaune" Cikin jin haushi tace"ke dai wai Maman Aisha wata irin mata ce,kai tir da uwa irin ki"ta faɗa tana mikewa"ace baka san in da danƙa ke aure ba,Allah dai ya basu zaman lafiya "ta faɗa tana wucewa. Kallon Mama tayi"hmmm adaiyi zaman lafiya mu gani," Ta faɗa tana ƙara fashewa da dariya, Bata bata amsa ba sai ma mikewa da tayi tana barin gidan bikin ganin hankalin mutane ya fara dawowa kan su,gara ta tafi ta bar mata gidan bikin kafin taja mutane su fara saka mata baki, Wanda ta lura haka take so, Maganar gaskiya hankalin ta ya tashi da maganar Maman momy,sai dai kawai idan ta tuna sunyi magana da Sumayya sai taji sanyi,amma bata San me yasa ba gabanta ya faɗi da maganar matar na yanzun, A baiyane tace"ya Allah ka kare min ya'ya na a duk in da suke". _____________washegari ƙarfe biyu na rana jirgin su ya sauka a Abuja, Suna fitowa Airport ya kalle ta"kina jin yunwa? Girgiza kai tayi, "Ok to bari mu tafi Minna kawai " Shatar mota ya daukar masu wanda basu suna shigo garin Mina ba sai kusan biyar da rabi saboda rashin kyaun hanya, Tunda suka shigo Chanchaga ta buɗe idanun ta,Addu'a take a zuciyar ta,Allah yasa kar ya kai ta Hotel, Ita dai taga yana ta ma direban kwatance har suka iso wani babban estate wanda taga a jin wani signboard an rubuta Talba Estate, Unguwar ta bayan gari yake babu hayaniya sai manyan gidaje, A ƙofar wani babban gida mai get taga yace mutumin ya tsaya, Shi da kanshi ya buɗe mata mota ta fito sannan ya saka hannun shi a ta jikin kofar gidan sai gashi ya ciro makulli, Budewa yayi ya mika mata key din"ki fara shiga bari na shigo da kaya " Kallon shi take tana kallon gidan......... *🍂JAURO🍂* (MAI ANGUWA) Story & Writing By JIDDARH UMAR 🌟🌙🌙🌙🌙🌙🌙🌟 *🌙✨MOONLIGHT WRITER'S ASSOCIATION🌙✨* https://m.facebook.com/Moonlight-writers-association-109698351308376/ *'''We are the moonlight writers we shine all over the world.''🌍'* ✍️✍️ بِسم الله الرحمن الرحيم ~~~~~~~💞💞~~~~~~~ *Ban yarda wani ko wata su saka min littafi a shafin su ko su mai da min littafi Audio ba tare da izini na ba* *41* *Wannan littafin nawa mai suna a sama na mai da shi na kuɗi,tare da Yar Tsanar Zinare,wanda yake son guda ɗaya dari uku 300,guda biyu 500 dari biyar, Hauwa Umar,Zenith Bank,2284905309,sai shaidar biyi ta wannan number 08141644865* Ganin ya juyo da katon jakka ne yasa da sauri ta tura kofar gidan ya buɗe tana matsa mai ya shiga, Binshi tayi a baya har ƙofar falon shiga inda anan ma sai da ya ƙara buɗe ƙofar sannan suka shiga, Tsayawa tayi ta sake baki a tsakiyar falon tana kallon Aljannan duniya, Falon babba ne wanda yake dauke da saitin kujeru manya manya masu numfashi har saiti biyu,ta gefe ɗaya kuma harda Dinner table,gashi ko ina yaji manyan labulaiya,Dark Blue da fari, Gaskiya falon ya haɗu iya haɗuwa domin duk da ba wasu tarkace ne a falon ba amma da ka ganshi kasan yaji kudi, Titowa yayi daga ɗakin da ya kai mata kaya ya zo ya same ta inda ya bar ta tsaye"ga ɗakin ki can na kai maki kaya"ya faɗa yana fita domin kwaso sauran kayan, Bin hanyar da ya nuna mata tayi domin ta Allah_Allah take taga dakin da yake fadin nata ne, Babban ɗakin ne mai dauke da Royal bed mai dauke da durowar madubi,sif din saka kaya,abin rataye jakka wurin saka takalmi,harta inda aka daura TV na gadon ne,sai firij ƙarami da kushin guda buyu wadanda daga ganin saitin kasan duk na gadon ne,kai ko ban dakin abin kallo ne,dakin yanda kasan dakin yar wata babban mai kuɗi, Zama tayi saman kushin din tana sauki nunfashin gajiya,da sauri kuma ta mike jin zuciyar ta ya raya mata to idan gidan ba nashi bane fa,kai yaga kudin gina irin wannan gidan,bari dai ta je ta tambaye shi,in ya so komai dare Gara ya maida ta inda zasu zauna ba zata kallon irin wannan kwalelen ba, Tana saka kai shi kuma zai shigo,karo suka yi,da sauri ya koma baya yana ya mutse fuska, "Ki dinga kallon gaban ki Sumy Baby" Shafa goshinta tayi"ni dai kazo ka mai dani gida" Kyara tsayuwar shi yayi"wani gida kuma kike magana wai bancin wannan " "Gidan da aka fara kai ni ma" Ƙaramin tsaki yaja"ba zan iya zama a can ba shi yasa na kama mana hayan nan gidan dan haka sai ki kwantar da hankalin ki" Waro ido tayi"kana nufin harda komai na gidan " Bai bata amsa ba sai ma cewa da yayi"ni zan fita akwai kayan abinci a kicin in kina buƙata sai ki Girka" Bai jira amsar ta ba ya juya yana ƙoƙarin fita, Ƙara dakatar dashi tayi"na ce ba" Wannan karon kamar ranshi a ba ce ya juyo,sai dai bai ce komai ba. "Ɗan Allah ina bukatar waya saboda ina son in yi waya da su Mama" Gani tayi kawai ya juya ya wuce ba tare da ya ce mata komai ba, Da kallo ta bishi,kome ke damun shi oho, Zagayen gidan take tana farin ciki,koda ma na haya ne abin ba karamin daɗi ya mata ba, Kicin ta shiga nan ma wata duniyar ce,kayan abinci babu irin wanda ba'a zuba ba, Taliya da kifi ta dafa,dan shine abu mafi sauki da zata iya dafawa yanzun, Tana kammalawa ana kiran sallah Magrib,dan haka wanka tayi da ruwa masu dumi, Tana fitowa durawar kaya ta buɗe duk da tasan babu komai aciki amma dai tana son ta gani ta kuma jera waɗanda ta siyo ma kanta a can, Sai dai ga mamakin ta sif din kaya ne a ciki na ban mamaki,duk da ba zata kira shi da acike yake ba,amma dai tasan ko atamfofi dinkakku manyan zannuwa bana roba ba sun kai kala goma,sai las uku shadda uku,sai jallabiyoyi sun kai kala biyar, Abin mamaki harda ƙanana kaya haddu irin wanda bata taɓa tsammanin gani ba, Rike baki tayi"eeye lallai ma Jauro ɗan duniya,kowa ye ya ajiye da zai saka mashi irin waɗannan kayan oho,"tsaki kuma taja"oh na manta ma ba amfani gare shi ba,waiyo Allah na Maman Momy kin cuce ni da kika haɗa ni da raggon namiji "jawo wani hijabi babba sabo tayi cikin kayan da ta gani,dashi tayi sallah sannan ta saka wani ƙaramin wando iya cinya,da riga mai dogon hannu ta robo,rigar ya matse ta sosai, Kyara suman kanta tayi ya sauko mata har gadon bayan ta, Masha Allah,yanda kasan wata Yar Tsanar Zinari, Fitowa falo tayi ta zuba taliyar ta a plate yaji kifi,ga lemun kwali a gefe,tana ci tana kurban lemu, Tunda ta aure Jauro bata taɓa cin abinci ta koshi ba irin na wannan lokacin,dan sai da taji babu wurin zubawa sannan ta hakura, Kyara wurin tayi sannan ta wanke kayan da ta ɓata. Ana kiran sallah Isha'i ta tashi tayi sannan ta dawo falo ta zauna tana kallo,har wuraren ƙarfe tara na dare, Ganin bai dawo bane yasa ta shige daki ta canja kayan barci zuwa karamin riga iya cinya da pant,sai wata doguwa wacce ake daurawa a sama, Tayi kwanciyar ta,babu jimawa barci yayi gaba da ita,cike da tunanin gida, Bai samu ya dawo ba sai wuraren sha ɗaya na dare,ya shigo ranshi a bace,domin daga ƙauye ya fito ba karamin tsiya suka kwasa ba da su Ɗan Fodio,dan su ba da kuɗin da za'a hada sunce ba zasu ba da ba,tunda ba uban su bane,shi kuma Yabbaleyda zuciya ta kwashe shi ya kaima Ɗan Fodio sanda,nan take faɗa ya kaure a tsakanin su, Ana cikin haka ne,sai ga ƴan sanda sun shigo cikin ƙauyen sun kama mutum biyu samari wai ana zargin su da yin garkuwa da mutane,kuma su din abokan Ɗan Fodio ne,hakan ne yaja kananun maganganu ya shiga tashi a karamin garin kafin kace me, Tofa shine Baffa Sanda ke cewa ai Jauro shi ya kawo ƴan sandan tunda bai daɗe da zuwa ba suka zo,kuma dan sunji ya gaisa dashi cikin harshen Turanci shi kenan wai ai baki suka haɗa, Inna Binta harda marin shi tayi tana tsine mashi albarka wai indai yasa aka kama mata ɗan ta wallahi ba zata bar shi ba, Ko gidan Malam liman bai jeba ya baro Rugan ranshi a bace. Kokafin yayi wanka ya kammala abinda zai yi ya kwanta har sha biyu da rabi tayi,dan haka addu'a yayi ya kwanta, Yaso ya samu barci ko kaɗan ne sai dai abin ya faskara dan sai juye_juye yake, Ji yayi an buɗe ƙofar anshigo babu sallamah hakan ne yasa ya tashi ya zauna yana ƙara hasken wutan ɗakin, Kallon ta yake yanda take tafiya jikinta ko'ina yana motsawa cikin jan rigar barcin data saka mai tafiya da hankali, Tana isowa faɗawa tayi a jikinshi ta rungume shi tana haɗa bakinsu wuri ɗaya tashiga tsotso, Tare da rungumo wayar shi, Ji tayi ya zareta daga jikinshi da karfi,yana mikewa tsaye da sauri yana shafa wuyan shi, Tashi tayi zata ƙara nufar shi ya dakatar da ita"me gaka kike yi Sumy Baby " Cikin wani irin azababben shauki dake taso mata wanda bata san na menene ba ta ce"ji nake tamkar in ban same ka ba zan mutu,marana da jikina duk wani iri yake min,zan mutu idan baka min wani abu ba" "Me kika sha? Ya tambaya yana jin wani irin raɗaɗi yana ratsa in da ta taɓa shi, " Ni babu abinda na sha,dan Allah Jauro ka taimaka min ji nake kamar zan yi hauka" Girgiza kai yayi"ki koma ɗakinki ki kwanta dare yayi" Kuka ta fashe da shi sosai "dama kasan ba kada lafiya shine kaje ka aure ni? Yanzun gashi ina cikin wani yanayi ka kasa yin komai," Mulmula ta hau yi a kasa tana kuka tare da riƙe ciki"waiyo Allah ciki na zan mutu " Da sauri ya matso inda take kwance,"ɗan Allah ki daina ta da min hankali da wannan kukan naki" "Mugu ba zan daina ba,kuma sai Allah ya saka min" Gabaɗaya hankalin shi a tashe yake,ya rasa yanda zai yi da ita,domin Allah ya gani bai san me yasa ba,in dai har zai taɓa ta ko ita zata taɓa shi to ji yake tamkar wuta ya taba,dan wani irin zafi ne zai ji yana ratsa jikin shi,ko inda hannun shi ya taɓa ajikin ta, Kuma abin ya fara ne bayan barowar su Centiago, A da ya dauka wasa ne,amma lamarin ƙara ta'azara yake,dan yaya ta taba shi ji yake kamar an daura mashi dutsen wuta a wurin,ko cika tsayawa yayi daf da ita sai ya dinga jin wani huci na zafi na buso mashi. Ita kuma gashi cikin lokaci kankani sha'awar ta ya karu,babu abinda take so sama da ya taɓa ta, A gaskiya besan me ya kamata yayi ba.......... *🍂JAURO🍂* (MAI ANGUWA) Story & Writing By JIDDARH UMAR 🌟🌙🌙🌙🌙🌙🌙🌟 *🌙✨MOONLIGHT WRITER'S ASSOCIATION🌙✨* https://m.facebook.com/Moonlight-writers-association-109698351308376/ *'''We are the moonlight writers we shine all over the world.''🌍'* ✍️✍️ بِسم الله الرحمن الرحيم ~~~~~~~💞💞~~~~~~~ *Ban yarda wani ko wata su saka min littafi a shafin su ko su mai da min littafi Audio ba tare da izini na ba* *42* *Wannan littafin nawa mai suna a sama na mai da shi na kuɗi,tare da Yar Tsanar Zinare,wanda yake son guda ɗaya dari uku 300,guda biyu 500 dari biyar, Hauwa Umar,Zenith Bank,2284905309,sai shaidar biyi ta wannan number 08141644865* Kamar wacce aka tsikara haka ta mike da sauri ta bar dakin, Bin bayanta yayi da sauri sai dai kafin ya isa har ta saka ma kofar key, Tun yana kwankwasa kofar yana Kiran sunan ta,saboda kukan ta da yake ji abakin kofa,har ya koma bubbuga kofa"Dan Allah Sumaiya ki bude min kofa, please" Cikin shakewar murya tace"go away,I don't wanna see you" Dafe goshin shi yayi yana jin yanda zuciyar shi ke zafi,"please Sumaiya ki taimaka ki bude min I am sorry i can help you with something" "I don't want your help,go away"tana fada tana buga kafarta da kofar da karfi, "Inna'lillahi wa'inna'ilaihi rajiun"ranar yanda ya ga safe haka yaga dare,domin kuka take sosai akan ciyon cikin,abinda ke bashi tsoro yana tsoron rasata,domin Allah ya gani ba karamin so yake ma Sumaiya ba, Tashin hankalin ta tamkar nashi ne,ranar anan bakin kofar dakin ta ya kwana idanun shi biyu, Kiran sallah Asuba ne yasa ya tashi dole sai da yayi wanka sannan ya tafi masallaci saboda yanda yake jin jikin shi babu dadi,ga stress daya kwaso a kauye ga kuma na rashin barci,duk da shi wanna ba damuwar shi bane tunda ai shi namiji ne akan ka, Ya tsayar da zuciyar shi in dai har ya dawo masallaci bata bude kofar nan ba to wallahi sai ya karya kofar, Dan haka koda zai tafi ma saida ya kwankwasa mata kofar kafin ya tafi, Ya dan jima a masallaci kafin ya shigo dan sai gari ya dan fara haske saboda Azkar din da ya tsaya yi, Ko dakin shi bai shiga ba kai tsaye kofar dakin ta yayi,sai dai yana taba kofar yaga ya bude,da sauri ya karasa tura kofar ya shiga dakin wanda yake da duhu, Wayarshi ya ciro acikin Aljihu ya kunna wutar dakin,nan take dakin ya dau haske, Hangota da yayi dunkule saman gado ne yasa cikin hanzari ya karasa in da take kwance, Hawa yayi kan godon yayi yana yaye bargon data rufa dashi,yana kallon kyakkyawar fuskarta fari tas wanda a yanzun ya koma jawur ya kumbura,tamkar yanda idanun nunta yafi ko in kumburi,ta gefe guda Kuma sai zufa take amma kamar sanyi take ji, Hannun shi har rawa yake kafin da kyar ya samu ya taba goshinta,duk da hannun shi na sauka akan fatar ta ya dauke da sauri, Ba zan iya tantance yanayin temperature din ta ba, saboda yanayin da jikinshi ke kasancewa,dan haka ya yanke shawaran gara ya mata physical examination,ya duba lafiyar matarshi tunda duk maganar da yake mata taki kulashi,yama gode Allah data bude kofar, Ya na gama duba Respiration ya sauka kan gadon don ba damar ya dau puse,yana shiga daki ya dauko digital thermometer ya dawo dakin,dashi yayi amfani yadau temperature din ta wanda anan ne ya fahimce irin zafin da jikinta yayi, Bazai iya taba taba,ta yaya zai taimaka mata,ta wata hanya, "Sumaiya, Sumaiya"shiru bata bashi amsa ba, "I know you can hear me, please tashi muje Asibiti," Jan bargon ta karayi"ka kyale ni babu in da zanje,Kuma ni lafiya ta kalau" "I know lafiyar ki kalau,Amma ni ba nida lafiya tashi ki raka ni Asibiti" "Bazanje ba" "Baki son in samu lafiya ne,na dinga biya maki bukatar ki" "Bana so,bukatar ma taka bana yi, live me alone" Kara marairaicewa yayi"nifa mijinki ne,dan Allah nace" Kuka ta saka domin ita kadai tasan yanda take ji,gabadaya jikinta ciyo yake mata,ga maranta kamar zai fashe dan ji take tamkar an ajiye mata dutse a mara, Ga kanta dake mata ciyo ta gefe daya, "Ni ka kyale ni,babu in da zanje"ta fada da irin muryar dazai tabbatar maka mutum bai da lafiya" Ajiyar zuciya ya sauke yana sauka kan gadon ya fita dakin,can babu jimawa kuma sai gashi ya dawo dauke da kofi a hannun shi, "Tashi kisha wannan" Kin kulashi tayi,shi gabadaya ma he is confused,ya rasa me zaiyi, Lumshe ido yayi ya bude,dan haka dagota yayi gabadaya jikinshi ya rungume ta,yana daure fuska tare da kafa mata kofin shayin abaki, Dago kai tayi tayi domin tayi musu,sai dai ganin yanda ya hade fuska da yanda idanun shi suka yi ja ne yasa bashi ta shiga kurban shayin a hankali tana hadiyewa da kyar, Sai da ya tabbatar da ta sha yakai rabin kofin kafin ya jingina mata filo,yana kyara mata zama, Yana fita kicin ya koma ya ajiye kofin kafin ya koma dakin shi ya shige bayi, Zame jallabiyan jikinshi yayi,yana kallon yanda Hannun shi daya rungumeta dashi ya tashi,wurin yanda kasan wanda ruwan zafi ya zubar ma haka fatan wurin yayi,ga radadin azaba da yake ji,harma a kirjin shi, Fitowa yayi ya bude jakkan aikinshi ya dauko wani oiltiment ya shafa a wurin, sannan ya maida rigarshi, Jin wayarshi na kara ne yasa ya dauka,sai kuma ya har kofar gida ya bude, Wata mata ce ta fito a cikin mota tare da wani matashin yaro,wanda daga dukkan alamu direba ne, Sai da ya gaida jauro sannan ya koma cikin mota yana jiran matar,ita Kuma tabi bayan shi.... *🍂JAURO🍂* (MAI ANGUWA) Story & Writing By JIDDARH UMAR 🌟🌙🌙🌙🌙🌙🌙🌟 *🌙✨MOONLIGHT WRITER'S ASSOCIATION🌙✨* https://m.facebook.com/Moonlight-writers-association-109698351308376/ *'''We are the moonlight writers we shine all over the world.''🌍'* ✍️✍️ بِسم الله الرحمن الرحيم ~~~~~~~💞💞~~~~~~~ *Ban yarda wani ko wata su saka min littafi a shafin su ko su mai da min littafi Audio ba tare da izini na ba* *43* *Wannan littafin nawa mai suna a sama na mai da shi na kuɗi,tare da Yar Tsanar Zinare,wanda yake son guda ɗaya dari uku 300,guda biyu 500 dari biyar, Hauwa Umar,Zenith Bank,2284905309,sai shaidar biyi ta wannan number 08141644865* Har ɗakin da take kwance ya kai ta,cikin tsananin damuwa yace"sister Hadiza dan Allah ki taimaka min ki yi mata treatment,taki yarda da ni" Murmushi matar tayi"kar ka damu Abdul Aziz,insha Allah zata samu lafiya "ta fada tana ƙarasa shiga ɗakin, " Na gode,"ya faɗa yana juyawa ya bar masu ɗakin, dan ya yarda da sis Hadiza in dai wurin iya creating interpersonal relationship ne da patient,yanzun zata saka ya saki mutum ya saki jikin shi da ita. Komawa falo yayi ya zauna yana fuskantar kofar ɗakin. Da sallamah ta shiga karasawa bakin gadon duk da tana da tabbacin a irin yanda ta kwanta ba lallai bane ta amsa mata,koda ta amsa ba lallai bane ta ji, A hankali ta yaye bargon dake jikinta wanda ta rufa dashi,tana kiran sunan ta, Amsawa tayi jin muryan mace tana buɗe idanu a hankali, Ganin matar ta mata murmushi ne ta kara buɗe idanun ta, Shafa fuskarta tayi "sannu kin ji,Allah ya baki lafiya,gashi kuma jikin naki da zafi sosai which is so bad,amma karki damu bara na taimaka maki," Ta faɗa tana taimaka mata ta jinginar da ita jikin gado,cikin sakin fuska ta nuna gadon"zan iya zama? Da ido ta amsa mata dan ji take har ta kanta Sara mata yake, "Yauwa na gode yar Albarka, Ni suna na Dr Hadiza Umar,ni likitan mata ne,wurin aiki na daya da Mijinki Abdul Aziz,ya min bayanin duk abinda ke damun ki,da taimakon Allah zaki samu sauki,dan wannan ba komai bane ni ma na taɓa shiga irin wannan yanayin da kike ciki shekara uku da suka wuce "nan ta shiga yi mata hira tana haɗa Allurai,tare da kwantar mata da hankali har ta samu tai mata,sannan tace ta kwanta ta huta idan ta tashi zuwa yamma zata dawo ta duba ta, Tun tana kallon matar sama_sama har barci ya dauke ta, Ganin tayi barci ne yasa ta fito falon in da ta same shi zaune, Da sauri ya taso yana tambayar ta ya jikin nata, " Ka kwanta da hankalin ka na mata duk abinda da ya dace,sannan akwai magunguna zan aiko Sani dashi ya kawo maka,zuwa yamma zan dawo" Godiya ya shiga mata har ta rakata bakin mota suka wuce sannan ya dawo,ya shiga dakin da take, Tsugunnawa yayi a gabanta yana kallon yanda ta faɗa lokaci guda, Yana son ya taɓa ta sai dai shi kan shi ya san bazai iya ba,dole idan ta tashi tana buƙatar wanda zai taimaka mata, Tashi yayi ko canja kaya bai yi ba naga ya fito falon,wata kofa yabi a cikin falon wanda ya fitar dashi ta bayan gida in da anan naga jerin motoci guda uku masu matukar kyau, Buɗe daya yayi ya shiga ya ta da ita,sannan yana zuwa bakin get ya fita ya buɗe get din sannan ya fita da motar,nan ma sai da ya ƙara tsayawa ta kulle, Sai da ya fito daga cikin unguwar sannan ya fara tunanin tsayawa ta siya mata abu, A Blue Mart ya tsaya ya siya mata ice cream dasu cake,harda shawarma,sannan ya karasa Dutsen kuran Hausa,inda anan gidan su Aunty Amina yake, Yaro ya aika akan yamai sallamah da mijin ta, Babu jimawa kuwa sai ga yaro ya dawo wai bayanan yanzun ya fita, Cewa yayi yaron yaje ya amso number shi, Aikuwa sai gashi ambashi a rubuce ya kawo mai, Bai bata lokaci ba ya shigar a wayar shi sannan ya danna kira,wanda kara biyu yayi aka ɗauka, Sallamah yamai suka gaisa sannan yake sanar dashi mijin kanwar matar shine Jauro, Kasancewar sun taɓa haɗuwa sau daya sai kuma ranar ɗaurin aure "ohh Jauro ya kake ya gida,ya kuma Sumayya da fatan tana lafiya? " Lafiya kalau,dama wata Alfarma nazo nima a wurin ka" Dan shiru yayi yana nazari a zuciyar shi,dan wallahi in dai kudi ne bazai ba shi ba koda rance ne yanda gari tayi zafin nan, Nan take ya rage fara'ar fuskar shi"ina jin ka" "Yauwa dama in babu damuwa so nake ka bamu aron Aunty Amina ita da yara su je ma Sumayya yini,dan ba ta da lafiya idan ta ganta kuma zata ji daɗi" Ajiyar zuciya ya sauke jin ba abun da yake tunani bane "a'a babu damuwaJauro,sai dai ni ba ni da kudin motar da zan bata har zuwa ƙauyen ku gaskiya" Jinjina kai yayi,yana mamakin mako irin na mutumin,gashi dai yana da rufin asiri dai dai gwargwado,sai dai kullun cikin kiran babu yake, "Ok babu damuwa dama ni ma gani a ƙofar gidan na dauka kana nan ne shi yasa nazo da kaina" "To ba damuwa hakan yayi," "Na gode sosai,sai anjima" "Yauwa" Ya faɗa yana kashe wayar. Shikuma wani yaron ya ƙara aikawa akan yaje ya ce ana sallamah da Aunty Amina in ji Jauro. Ko mintina uku ba'a yi ba sai gata ta fito da sauri har katon hijabin da ta saka yana tadiyeta, Karasowa tayi inda yake baki buɗe "Jauro kaine?ina sumaiya? Murmushi ya sake" Tana nan tana jiranki," Dan dakatawa yayi"kamar ya,tana nan dai lafiya ko? Wannan karon dariya yayi kaɗan ganin yanda tayi "karki damu tana lafiya,kinga shiga ki fito da yara,mun yi magana da mijinki yanzun ya yarda na kaiki wurin ta" Murmushi ne ya baiyana a fuskarta saɓanin da datsoro ke mamaye a fuskarta,"la yau zani na ga sumaiya,to bari nayi sauri na karasa shiri" Jinjina mata kai yayi, Har ta juya sai kuma ta ƙara juyowa Dan Allah ka jira ni karka tafi, Cikin tabbatarwa ya jinjina mata kai. Cikin sauri ta karasa yin abubuwa da zata yi, Allah yasa week end ne duk yara na gida,dan haka tare suka fito suka same shi cikin mota zaune yana jiran su, Ita kanta tayi mamakin ganin shi da mota,dan haka ta yi tunanin kila na abokan shi ne ya ara, A maimakon taga sunje wani wuri sai gani tayi sun shigo cikin unguwar su,kasa daurewa tayi "A'a Jauro ni kan Sumayya tana gida ne? " A'a so nake mu ɗauki Aisha mu tafi da ita " Dariya tayi"kace dai ana ji da Sumayya,yau mama sai tayi farin ciki " Shima dariyar yayi, Aunty Amina ce ta shiga da kanta ta fada ma Mama,sannan tazo tace ya shiga su gaisa da Mama, Ba karamin daɗi yaji ba da irin addu'ar da Mama ta mai,har da zai wuce ya ajiye mata dubu biyar, Ya kuma roƙi dan Allah ta bari Aisha tai masu week end a can, Cikin sauki ta amince,dan so take ko ba komai ta san halin da ƴar ta ke ciki,sannan Sumayya ma zata ji daɗi, Haɗa mata kaya tayi kala biyu a leda baki ta bata,sannan suka wuce, Surutu kawai yaran ke yi a mota wanda hakan ba karamin daɗi yake mashi ba,yana fatan wata rana yaga yaransu tare da sumaiya, Ita dai Aunty Amina kallon hanya kawai take yi ta yanda nan gaba ko da zata je zata iya gane hanya, Sai dai gani tayi suna bin hanyar lafiyayyen titi,har suna iso Estate ɗin,kafin taga sun yi parking a bakin kofar wani babban gida madaidaici, Fitowa yayi ya buɗe get ya shigar dasu har wurin ajiye mota kafin ha juyo yace"ku fito mun iso, bari na kulle get "bai jira cewar su ba ya koma in da ya kulle get din sannan ya dawo inda suke tsaye suna kallon gida, " Muje Aunty Amina " "To ta ce tana ƙara kallon ko'ina," Buɗe ƙofar falon yayi suka shiga yayin da wani ni'ima taccen kanshi da sanyin AC ya masu maraba, Su dai bin bayan shi suke yi har ƙofar wani daki"Bismillah muje tana ciki" Tare suka shiga,inda har yanzun take kwance saman lafiyayyen gado tana sharan barci,dan har ta yaye bargon dake jikin ta, Wani irin sanyayyan ajiyar zuciya Aunty Amina ta sauke,dan sai yanzun hankalin ta ya kwanta,dan wallahi da jinin ta a kumba yake, Karasawa tayi da sauri in da take kwance wanda kafin ta isa ma har yaran sun rigata rugawa da gudu sun faɗa kan Sumayya suna kiran sunan ta da suke kiranta dashi wato Ummin mu,suna jijjigata, Shi kuma Jauro ya karasa kansu yana sauke su daga jikinta"karku karya min mata bata da lafiya " Dariya Aunty Amina ta saka"ni dai banga alamun ciyo ba nan sai dai raki irin na sumaiya " Jin nauyin an danne ta da hayaniya ne yasa ta buɗe ido, Ai da sauri ta zabura tana rungume Samir,"da gaske kai ne? Jin an saka dariya ne yasa ta juyo,bata masan sanda ta ture Samir ba ta sauko da gudu tana rungume Aunty Amina dake mata dariya, Ganin haka ne yasa ya juya ya bar dakin fuskar shi dauke da murmushi. "Aunty Amina anya ba mafarki nake ba" Dan mintsininta tayi, Ihu tayi tana shafa wurin, "To kinji ba mafarki kike ba,mijinki ne ya dauko mu" Aisha ce ta hau buga kafa "Aunty Sumayya ni ce kaɗai baki so da baki rungume ni ba" Dariya ta saki na farin ciki tana jawota jikinta ta rungume ta"yi haƙuri autar Mama ban ganki bane" Shigowar shi ne ya katse su,yana ajiye manyan ledojin dake hannun shi,"Aunty dan Allah idan tayi wanka sai ta fara cin wani abu anan akwai ledan magani ki cire mata tashi," "An gama ƙanina" Ta faɗa fuskarta dauke da murmushi, Kara fita yayi, "Kai tunda baki iya bani wurin zama ba ni kan bari nayi karan banin zama kan kushin" Dariya tayi tana jawota suka zauna kan gado "duk cikin murnan ganin ku ne" Jin motsin leda ne tasa Aunty Amina juyawa tana fi ɗin "Amira bana hana ki taɓa abinda ba'a aiki ki ba,wa yace ki taɓa ledar " "Kai Aunty Amina ki kyale ta, kawo na buɗe maki" Ita da Aisha ce suna dauko ledojjn, "To kinga har da ƙaramar uwa ma tana son abun cikin ledar"dariya suka saka, Ciro kayan kwalamar dake ciki tayi ta zuba masu a gaba," Aunty Amina bari naje na yi wanka" "Ok sai kin fito ki dai yi sauri dan yau kan akwai hira" Da sauri ta shige bayi tayi wanka tana jin karfin jikinta na ƙara dawowa ga kuma farin ciki da take ciki, Tana fitowa ko mai bata shafa ba ta saka doguwar riga na jallabiya ta dawo ta same su,zama tayi suka ci kwalamar tare harda Aunty Amina suna yi suna hira, Sannan tasha magani, "Aunty Sumayya ki kunna mana kallo,naga kayan kallo a falo" Mikewa tayi"to muje"kallon Aunty Amina tayi"ina zuwa Aunty " "A'a bari na taso ni kan ki kai ni naga gida da kyau" "To mu je" Tare suka fito ta kunna ma yara TV, sannan suka fara shiga kicin, Buɗe baki da ido tayi"masha Allahu,kai kai kai,Sumaiya,wannan duniyar duk kicin ne," Dariya ta shiga yima Aunty Amina,ganin irin santin da take yi, "Kicin ne mana Aunty Amina,ga wurin girki" "Kai Alhamdulillah Allah mun gode maka,waɗanda suke tunani zamu sha kunya su ne da kunya,dama Jauro na da irin wannan dukiyar shine ta ɓoye mana? Dazu kinga kuwa a irin motar daya dauko mu?Allah na gode maka hutu yazo" Tabe baki tayi tunda ta ji ta ambaci sunan shi,"muje mu gani dan nima ban ga gidan ba" "Ke da gidan ki kice baki gama gani ba" "Jiya fa muka dawo daga England" "Kai Sumayya ban da karya" Juyowa tayi "wallahi da gaske nake,muje dai mu gama gani,amma akwai labari" "Shi kenan muje,amma har na matsu mu je" Sun zagaya gidan sosai dan ita kanta tayi santin gidan sosai,kafin su dawo cikin dakin ta, Zama tayi kan gado tana nishi, "Ke ni bani labarin me ya faru bayan mun kaiki wancan gidan," Ajiyar zuciya ta sauke,sannan ta shiga bata labarin tun daga kaita da sukayi da zamansu a Hotel har zuwan su England da dawowar su,"Aunty Amina har yanzun na kasa sanin asalin waye nake aure,na kasa sanin halin shi,me ya mallaka menene a rayuwar shi,shi din wani irin mutum ne,har yanzu na kasa sani,wani lokacin idan yayi wani abun ki na ganshi da wani abun har mamaki yake ban,na rasa gane inda rayuwar shi ya dosa" Ita karan kanta nazari take yi "to wannan gidan fa? " Da fari da muka zo ya ce min na shi ne,daga baya dana matsa mai yace wai na ogan shi ne" "Amma ke a naki hasashen ta kike gani" "Ina ganin na shi ne kawai,dan a yanda na lura yana da kudin kawai bai son nuna wa ne" "In dai har da gaske na shi ne,ba damuwa,sai dai ina son kibi mijinki a hankali domin ki gano da wani irin mutum kike zaune,bawai sai kin fara tara iyali dashi ba,sannan ki fahimce waye shi,a lokacin kuma lokaci ya kure maki,dan haka cikin sanyi,dubara,sakin fuska,zaki iya fahimtar shi,ku kwantar da kanki,na tabbata cikin sauki zaki gano komai dangane dashi saboda na hango soyayyar ki sosai a idanun shi,idan har kika ci nasara akan komai Sumayya,na tabbatar hakan tamkar narasan mu ne ni da Mama,domin zaki taimaka mata," Cikin damuwa tace "Aunty Amina bana son shi ko kaɗan,har yanzu bana jin son shi" "Ko da baki jin son shi,ki dage da addu'a Allah ya saka maki soyayyar mijinki,shi kuma Allah ya ƙara mashi soyayyar ki a zuciyar shi,in sha Allah komai zai yi daidai,koda ace komai ba nashi bane,idan har kin mallaki soyayyar shi duk abinda ya mallaka ko mai ƙanƙantar shi zai zama naki,na ki ƙara godewa Allah shi ba mugun mutum bane kamar Baban Samir,shi yasa Hausawa ke cewa saka auri me dukiya gara ka auri mai zuciyar yi, An aura maki shine da manufar mai da je karamar bazawara ta yanda za'a ƙuntata zuciyar mahaifiyar mu, Tunda baki son shi ai dole zaki kaso auren a tunanin su,dan Allah Sumayya ki basu kunya,ki zauna da mijinki lafiya,kar ki yi abinda zuciyar mahaifiyar mu zai gaza ɗauka " Rungume Aunty Amina tayi hawaye na bin idanun ta"na maki alƙawarin zan zubar da komai,insha Allah,zan saka ku Alfahari da ni kada mama,zan kuma bi muku hakkin ku a wurin mazajen ku " Murmushi tayi itama tana share nata hawayen "Allah ya maki Albarka ta kuma jagoranci rayuwar ki" "Amin" Ji suka yi ance"Mama yunwa nake ji" Duk kallon Samir suka yi dake tsaye a bakin ƙofa "to kaje gamu nan zuwa" Girgiza kai tayi"yaro baya jimirin yunwa" "Kai kalli Agogo Aunty Amina har sha biyu tayi,ashe mun daɗe zaune" "Ai lokaci ba wuya yake gudu yanzun" "Bara to nake na daura mana ko da Cos_cos ne" "Muje dai ki nuna min yanda zaki ake amfanin da Gas,sai na girka mana tunda ba lafiya ne dake ba" Tare suka shiga kicin suka yi girkin wanda yaji zuku_zukun nama, Zuba ma Jauro na shi suka yi a kula nasu kuma suka hada a babban pleta da yara,suka baje a falo suna ci suna hira, Aunty Amina ce tace"ke tashi ki kaiwa mijinki na shi," Turo baki tayi "bari na gama cin nawa tukunna" "A'a wallahi baki isa ba,tashi maza" Tana turo baki ta mike zata nufi kicin sai gashi ya fito cikin wannan dai shigar tashi data tsana,daga dukkan Alamu sauri yake" "Sannun ku Aunty na" "Yauwa sannan kanina" "Sumy Baby zan fita,ko akwai abinda kike buƙata,? " A'a,sai dai ga abinci an gama" "Yauwa to saka min a kwando sai ba tafi dashi,dan nayi baki ne kuma suna jira na" Kicin ta shiga ta saka mashi a kwando har da cokula,da lemun kwali guda biyu da plate, ta kawo mashi" "Na gode ya faɗa yana ansa" "To sai ka dawo" Cikin jin daɗin maganar ta yace "Thank you" "Aunty zuwa yamma zan dawo na maida ku gida" "To ƙanina sai ka dawo,Allah ya tsare" Da Amin ya amsa yana barin gidan. Can gidan gonan shi dake maikunkele ya nufa inda anan suke jiran shi, Ba ƙaramin farin ciki ganin su yayi ba,dan rabon shi da su shakara biyu kenan tun dawowar shi karatu, Wato masu su Haruna,waɗanda yanzun kan manyanta,shekara ishirin ba wasa ba,tun kafin rasuwar mahaifinsa Baffa Dottiya da ya basu Amanar Dabbobi shi,basu kara dawowa ba sai sheka biyu ba suka wuce da suka zo suka kawo mashi dukiyar shi da mahaifinshi ya basu amana wanda tayi Albarka sosai,fiye da tunanin shi, Sunyi kukan mutuwar uban gidan nasu sosai suna tuno Alkhairin shi shida Uwar dakin su,mutuniyar kirki. Da zasu tafi kuma ya masu abinda Arzikin da basu zata ba,kuma ya biya ma su biyun kujeran makka, Nan suka mai bayanin komai,wanda shine dalilin buɗe wannan gidan gonan da yayi,ko lokacin da suka je da Sumaiya bai dai kai ta Asalin inda ake noma da kiyo bane,domin da kashin shanun shi suke amfani wurin yin takin su, Iya karta wurin kiyon kaji, To sai wannan lokacin da suka kawo mai ziyara, A cikin wani kayataccen wurin hutawa dake cikin wurin wanda aka kayatashi da lambu suke zaune tare dashi suna hira bayan sun kammala cin abinci, Haruna ne yace"nikan Jauro meke damun ka ne " Murmushi ya kakalo"babu komai " Kallon shi yake sosai "faɗa min gaskiya,domin ga jikinka nan naga yana hayaƙi" Kallon kan shi yayi cikin mamaki yace"haya ki kuma" Dafa kafadarsa yayi"muna da wankin ido,saboda dajijjikan da muke shiga,baka San me zaka haɗu dashi ba,tunda ka shigo naga jikinta na haya ki,ka faɗa mana komai zamu taimaka maka" Ajiyar zuciya ya sauke,sannan ya shiga sanar dasu lamarin dake faruwa tsakanin shi Sumayya "sam bana iya taɓa ta duk yanda naso,dan ji nake kamar zan kome" Shiru suja yi suna sauraran bayanin shi har ya kammala, Sannan,Isma'il yace.......... *🍂JAURO🍂* (MAI ANGUWA) Story & Writing By JIDDARH UMAR 🌟🌙🌙🌙🌙🌙🌙🌟 *🌙✨MOONLIGHT WRITER'S ASSOCIATION🌙✨* https://m.facebook.com/Moonlight-writers-association-109698351308376/ *'''We are the moonlight writers we shine all over the world.''🌍'* ✍️✍️ بِسم الله الرحمن الرحيم ~~~~~~~💞💞~~~~~~~ *Ban yarda wani ko wata su saka min littafi a shafin su ko su mai da min littafi Audio ba tare da izini na ba* *44* *Wannan littafin nawa mai suna a sama na mai da shi na kuɗi,tare da Yar Tsanar Zinare,wanda yake son guda ɗaya dari uku 300,guda biyu 500 dari biyar, Hauwa Umar,Zenith Bank,2284905309,sai shaidar biyi ta wannan number 08141644865* "Wannan aikin sihiri ne,wanda akayi domin a raba ku,ta yanda ita aka saka mata matsananci sha'awa kai kuma aka saka maka jin zafin jikinta,ta yanda ba zaka iya taimaka mata ba,daga karshe ita kuma dole ta shiga bin maza domin sabon abinda bata samu ba daga gareka,a takaice dole zaka sake ta daga karshe,wannan shine ma'anar wannan Asirin da aka muku" Gabaɗaya hankalin shi tashi yayi tunda yaji an sako sumaiya ta bi wasu maza,shi kuma zai sake ta, Ji yayi wani abu mai ɗaci ya makale masa a makoshi, Cikin tsananin kishin da shi kanshi bai san yana da shiba a kanta yace"wallahi Baffa Haruna da kuwa na kashi duk wanda yayi ƙoƙarin rabar matata,koda kuwa waye shi,na rantse maka da wanda raina da numfashina ke gare shi idan hr hakan zai faru to ba zan iya jurewa ba" Dafa kafadarshi Baffa Isma'il yayi"ka daina ma fadar haka,domin da yarda Allah hakan ma ba zai faru ba,tunda har mun san komai ka sa a ranar komai ya zo ƙarshe,ina nufin matsalar ka, Yanzun fada min,idan anyi aikin so kake amai da ma wanda yayi ko kuma a kyale shi? Sai dai ina mai tabbatar maka idan har aka kyale shi ko ita,to tabbatar gaba ba'asan abinda zasu yi ba,me ka gani? Ba tare da wani dogon nazari ko tunani ba yace"a maida ma wanda yayi aikin shi"domin shi tunda yaji an ambaci Baby shi taba wasu mazan ya rasa hankalin shi, Juyo da kanshi Baffa Isma'il yayi gare shi,dan ya lura kamar duk baya cikin natsuwar shi,"ka yarda dani? Ya tambaye shi yana kure shi da ido, Ajiyar zuciya ya sauke,yana ƙoƙarin sai saita kan shi,"kun dauke ni tun daga randa na fado duniya,duk da banyi tsayin rayuwa da kuba,kun rike alkawarin mahaifinna baku ci amana kun manta dani ba,ko da ace ɗan da kuka haifa ne ni iya abinda zaku mai kenan,shi yasa nake nake maku kallon amintattun iyaye,na yarda daku fiye da yanda na yarda da kaina," Dukkanin su murmushi suke yi saboda jin daɗin kalaman shi, Gefen Darduman da suke zaune ya damko kasar wurin a hannun shi ya mika mashi "karɓi wannan kasar ka je ka zuba a banɗaki inda ake bahaya, aciki zaka saka,idan ka yi wannan Baffan ka Haruna zai kara sa maka sauran aikin nan da kwana uku," Amsar kasar yayi yana kallon shi a hannun shi,sai kuma ya mike da sauri ya bar wurin,dan wallahi bayin da katan masu kiyo ke kashi nan zai je ya zuba, Mintuna biyar ya dawo ya zauna "na kammala" "To yanzun akwai wasu addu'o'in da za'a baka wanda zaka lazimce yin su safe da marece,mu kuma zamu din ga tayaka da namu addu'ar,domin da ita muka dogara," "Insha Allah" "Nan Baffa Isma'il ya faɗa mashi yanda zai yi da kuma irin addu'o'in,wanda yace idan ya manta ya duba cikin Husnil Muslim" "Godiya ya masu sosai kafin su cigaba da hira. *A gida kuwa* Zuwa ƙarfe biyar har sun kammala girkin dare,dan Sakwara da miyar taushe suka yi,Aunty Amina ce ta daka sakwaran, Ɗaki taja Aunty Amina ta fito da katon jakkan da suka dawo dashi tafiya wanda anan ta saka nasu tsara ban, Fito da kayan dake cikin jakkan tayi tana warewa wasu gefe,kafin ta dauko wasu dogayen riguna guda uku ta mika mata"Aunty na wannan tsarabar ki ce ta England " Karɓar kayan tayi cikin tsananin farin ciki ta shiga buda kayan tana saka mata Albarka, Kafin ta miko mata na yaran ta harda na Mama,wanda nata a aciki harda turare, Kallon kayan maza dake gefen ta tayi"to ina na Baba"ta tambaya ganin tana ƙoƙarin mai da su cikin haƙƙin. Nan take ta bata fuska "ban siyo ba" Waro ido tayi tana kallon tsarabar data jido masu amma tace banda Baba,cikin mamaki tace"to me yasa" "Kawai dai,kinga mu bar maganar kema in baki so bani kaya na" Da sauri ta ƙara jawo kayan ta rungume dan ta san Sumaiya wani lokaci ba mutum ci ne da ita ba,"ba ki ji na ce haka ba,to amma maganar gaskiya kema kinsan ya kamata ki bashi wani abun" Cikin takaici ta kalle ta"wai Aunty Amina me kika dauke ni ne? Me kika mai da ni ne?to bara na sanar dake koda kuɗi na na jan ƙasa ba zan taba ɗauka na ba Baba a matsayin kyauta ba,ke har kin manta me ya mana,kin manta halin da kike ciki,wanda Uwar mu ke ciki,ni kaina nake ciki,Allah yamin tsari,in dai har na bashi to bansan darajan mahaifiyata ba kenan " Riƙo hannun ta tayi da sauri cikin kariyar zuciya,da kuma tsoron irin tsanar mahaifin su data hango a idanun Sumaiya,"ke kike faɗa haka ne Sumaiya,shi din fa mahaifinmu ne,y kama ki manta duk abinda ya faru a baya... Katseta tayi cikin jin haushi da hasala "na manta baya? Na manta baya da kika ce Aunty Amina,to gaba fa idan na manta bata,ya riga ya cuce rayuwar mu tun daga lokacin daya auri kawar mahaifiyar mu wacce bata san Allah daya bane,a gaban ki kin ga irin wulakanci da tozarci da maifiyarmu ta fuskanta saboda shi! An raba ki da mutumin ƙwarai dake ƙaunar ki,an haɗa ki mugun Azzalumin miji,kullum cikin duka da tsangwama,saboda kawai uwar mu ra haɗiye zuciya ra mutu!to bari kiji in ke kin manta ni ban manta ba,ranar daya buɗe baki a ban mahaifiyar mu yace mata daga ke har Yayanki ba kuda amfani a gare ni,domin in da ace a maza kika haife su da nayi Alfahari da su,amma kin haifamin abinda ba zasu amfana min komai ba,a lokacin da na isa shiga makaranta ki sakani yayi,da kudin sana'ar ta na shiga Boko,har na gama primary zan iya tuna sau nawa ya taɓa ban kudin break,haka ma secondary School,har izuwa NCE din dana yi,a lokacin da nake ganin na na kai matakin da zan iya dafa ma mahaifiyar mu,a wannan lokacin ya ƙara daƙile komai ya aura min mutumin da bai san daga ina yake ba, Amma da yake Allah ba Azzalumin kowa bane,sai gashi yanda suke fata bai samu ba,ke kalli halin da kike ciki amma amma har kina batun wani a manta baya,to ba da ni ba," "Sumaiya a dai rinka yafiya,domin ko Allah yace ina tare da masu haƙuri" Kallon uku saura kwata tai mata, tare da turo mata wani babban leda "kinga ga leda nan ki kwashe kayan, ku,na Aisha kuma ki barmin su anan,batun Baba kuma ki kyale ni dashi" "To uwa ta" Jin sallamah a bakin kofa yasa suka juya tare da amsa mashi, Sai da suka gashi izinin shigowa sannan ya shiga *🍂JAURO🍂* (MAI ANGUWA) Story & Writing By JIDDARH UMAR 🌟🌙🌙🌙🌙🌙🌙🌟 *🌙✨MOONLIGHT WRITER'S ASSOCIATION🌙✨* https://m.facebook.com/Moonlight-writers-association-109698351308376/ *'''We are the moonlight writers we shine all over the world.''🌍'* ✍️✍️ بِسم الله الرحمن الرحيم ~~~~~~~💞💞~~~~~~~ *Ban yarda wani ko wata su saka min littafi a shafin su ko su mai da min littafi Audio ba tare da izini na ba* *45* *Wannan littafin nawa mai suna a sama na mai da shi na kuɗi,tare da Yar Tsanar Zinare,wanda yake son guda ɗaya dari uku 300,guda biyu 500 dari biyar, Hauwa Umar,Zenith Bank,2284905309,sai shaidar biyi ta wannan number 08141644865* "Ƙanina barka da dawowa," Murmushi yayi yana ɗaukar Amira dake mai oyoyo "na dawo Auntyn mu," Ya faɗa yana kallon ta yanda tayi dai_daya daga ita sai towel daga dukkan alamu daga wanka ta fito, Mintsinin ƙafarta ta fara tana mata alama akan ta gaida shi, "Baby Sumy ya jikin naki? " Da sauƙi " "Kin sha magani kuwa? " Na sha " Kallon Aunty Amina yayi"Aunty na ku fito na kai ku gida dare na yi," "To gamu nan fitowa" Falo ya koma yana jiran fitowar su, Ganin ya fita ne yasa ta juyo cikin jin haushi ta kai mata duka"ke wai me yasa ba zaki taɓa yin hankali ba" Ihu tayi tana shafa wurin"haba mana Aunty Amina,to ni me nayi miki,kike cin zali na" "Me yasa da Mijinki ya shigo baki gaida shi ba,haba mana Sumaiya," Turo baki tayi tana kumbura fuska,"kawai dai haushi na kike ji saboda naki ba Baban ki tsaraba " "Sumaiya ni fa ba dan haka bane,kawai so nake naga kin san darajan mijinki tamkar ko wace macen kirki,dan Allah ki sauke kanki ki fuskanci rayuwa,yanzun fa kika gama faɗa min ba zaki bani kunya ba," "To ni me zan mishi" Ta faɗa a shagwabe, Dafe kai tayi "ohhh ni Allah na gode maka,wai sumaiya ina amfanin ma littattafan Hausa da kike karantawa,dana Turanci? " Ai waɗannan littafi ne kawai Aunty,wannan kuma zahiri ne,akwai banbanci,is not easy " "Na sani,amma ke a tunanin ki me fa'idar karanta littafi? " Dan nishaɗi "ta faɗa kai tsaye. Girgiza kai tayi" Kin yi kuskure kuwa da kika dauke shi a haka," "Kamar ya? Nifa wani lokaci kona fara karantawa sai na bar shi,wasu sun cika saka maganar banza" "Haka ne,amma ke ba da maganar banzan zaki yi amfani ba,sai ki dauki na kirki,bari na faɗa maki abinda baki sani ba,yana da kyau kome zaki yi a rayuwar ki ya kasance kina da dalilin yin shi,misali kamar karanta littafin Hausa,yawanci mutane suna ɗaukar shi ne kawai for granted,saboda nishaɗi,amma kuma da zasu duba sakon dake kunshe a cikin littafin zasu amfana dashi sosai,a cikin littafi mutane da yawa ke fuskantar rayuwa,a cikin littafi wasu ke gyara zamantakewar su da mazajen su,a cikin littafi wasu ke sanin yanda zasu kara samun kusanci da Ubangijin su,wasu da iyalansu,wasu kuma suke iya banbance abu mai kyau da mara ƙyau,wannan sabon Allah ne,wannan kuma halak ne wannan kuma Haram ne,na tabbatar da yawancin abubuwan wallahi wasu basu san su ba,sai idan an rubuta shi a littafi sai ki ji mutum yace,ohh dama haka abin yake,ko kuma kiga mutum na cikin matsala ya rasa mafita,amma Albarkacin wannan littafin Hausa cikin sauki ya samar ma kanshi masalaha,shi karanta littafi bawai yana koyarwa bane akan ka ɗauki mugayen ɗabi'un dake ciki bane wadanda ita marubuciya ta rubuta ne domin misali,kawai abin da ake so shine ka dauki abubuwa masu amfani dake ciki wadanda zasu amfanar da kai,kabar marasa amfani, Masana sun tabbatar da cewa duk wani abinda kwakwalwa zai iya tunani hannu ya rubuta to tabbatar zai iya faruwa kokuma ya faru,, Misali kamar kiga ace ta faɗa ruwa kaɗa ya haɗiye ta amma bata mutu ba,in ke baki gani ba,to wasu sun gani ya faru a wani garin ko wani ƙasar, Dan haka ina son kiyi tunani ki samar ma kanki mafita, ta hanyar kula da mijinki da sauke duk wani karya da girman kan dake damun ki,dan Allah sumaiya " Sauke numfashi tayi "insha Allah" Dazun ma haka kika ce amma gashi ko wucewa banyi ba kin karyata maganar ki" "Aunty da gaske nake wannan karon" Mikewa tsaye tayi tana daukar ledan dake hannun ta,"na gode sosai Allah ya ƙara maku fahimta ke da kanina," Bata ce komai ba ta amsa ledar tayi falo dashi, Girgiza kai kawai tayi tana mata addu'a a zuciyarta, Har bakin motar da zai kai su dashi ta raka su ita da Aisha sannan suka koma ciki, Alwalla suka yi sannan suka yi sallah,tana Idarwa ta saka doguwar riga wara nauyi, Aisha ce tace "Sumaiya muje ki kunna nin kallo" "Wato dai ke ba zaki daina kirana da Sumayya ba" Turo baki tayi"to me zan kira ki" "Aunty Sumayya mana zaki ce" "Babu daɗi wallahi Sumayya yafi daɗi" Duka takai mata"kaji shegiyar yarinya,babu kunya ki ce kiran suna na gatsau yafi maki daɗi? Ihu tasa tana komawa gefe"shi yasa bana son ki nafi son Aunty Amina" Zaro ido tayi tana nuna kanta"yanzun kinfi son Aunty Amina akai na " Jinjina kai tayi , "Saboda me? " Saboda kina cin zali na,shi yasa da kika yi aure nake ta jin daɗi " Salati ta saka"yanzun Aisha in da mutuwa nayi ma haka zaki rinka jin daɗi " Shiru tayi kawai tana kallon ta, Cikin jin haushi ta mike tayi kanta zata daka, Ita ko ganin haka yasa ta mike tayi falo da gudu tana ihun kiran sunan Mama, Kasancewar ita ma ba nauyi ne da ita ba yasa cikin sauki ta kamo ta, Ihu ta fara"nafasa kwanan ki mai da ni gidan Mama wacce bata duka na,ba zan yi hutun ba tunda duka na zaki rinka yi" Jin tace haka ne yasa ta rungume ta maimakon dukan ta da zata yi da"haka mana Aishan Mama,waya faɗa maki dama dukan ki zan yi,kawai dai wasa nake maki,dan na kwada ki" Make kafaɗa tayi"ni dai na fasa kwana " "Ke nifa wasa nake maki,kin ga zauna na kunna maki kallo,zaki sha Ice cream? Jin an ambaci ice cream yasa da sauri ta gyaɗa kai" Shafa kanta tayi "yauwa Autar Mama," Ta faɗa tana zaunar da ita sanan kushin sannan ta dauko mata ice cream ta kunna TV, "Wani tasha kike so? " Ki samin na Baby " Kunna mata tayi sannan ta zauna itama tana shan nata tana kuma janta da hira, Sai da yakai su har gida sannan ya dawo,shima zama yayi a falon yana hiran shida Aisha dan ita madan tunda ta gaida shi ta kawo mai abinci bata kara ce mashi komai ba, Ganin ƙarfe goma saura ne yasa ya ɗauki Aisha ya kai ta ɗakin ta ya kwantar kan gado sannan ya dawo in da take ya zauna,"kina buƙatar wani abu ne "ya faɗa yana kallon ta. Cikin basarwa tace" Ko na faɗa samu zan yi? Ta faɗa cikin yanayin tambaya. "Kika sani" Mikewa tsaye tayi"ni Barci nake ji sai da safe " "Allah ya tashe mu lafiya,I Love you" Jin abinda ya faɗa ne yasa ta juyo ta kalle shi cikin mamaki, Murmushi ya sakar mata,yana ƙara maimaitawa "i Love you" Da sauri ta juya ta shige daki ba tare data ce komai ba. Faɗawa tayi kan gado gefen Aisha tana sauke numfashi "kome ya shiga kanshi yanzun kuma ohho" Addu'ar Barci tayi ta tofe jikinta dashi sannan ta tofa ma Aisha tana ja masu bargo, Washegari da safe tunda suka yi Sallah ita da Aisha suka koma suka kwanta, Da ya dawo masallacin ya leka yaga lokacin suna sallah shima dakin shi ya koma ya kwanta, Wayar da aka mashi daga wurin aiki ana nimanshi shi ya tada shi, Wanka yayi ya shirya sannan ya shiga dakin ta, Cikin barci taji ana kiran sunan ta a hankali, Da kyar ta buɗe Ido saboda ji take kamar mafarki take,"tashi muyi magana " Mikewa zaune tayi,tana kallon shi da idanunta masu cike da barci, "An kira ni wurin aiki,amma ba zan daɗe ba zuwa ƙarfi goma zan dawo,dan ina son mu fita,dan Allah kafin in dawo kiyi kokarin ku shirya ke da auta" Da kyar ta iya cewa "To" ta koma ta kwanta, Har ta lumshe ido sai kuma ta buɗe, Idanunta ne suka sauka cikin nashi,daya kure ta da shi "zaka fita baka yi break fast ba" Bai san sanda ya saki murmushi ba,lailai Allah ya fara ratsa zuciyar Sumaiya, "idan na je office zan ci" "Shi kenan Allah ya tsare"ta faɗa tana maida idanunta ta lumshe tare da kara jan bargo. Murmushi yayi yana barin dakin. Tashinta da Aisha ke yi ne tana faɗin yunwa take ji shi ya tada ita, Idonta ne ya sauka kan Agogon daya nuna mata ƙarfe tara da minti ishirin, Ai bata San sanda ta fado kasa ba, Jan hannu Aisha tayi suka shiga bayi tare,maklin ta saka mata a sabon brush data buɗe mata ta bata,ita ma ta saka sannan suka yi, Hitan ruwan zafi ta kunta ta zuba mata yanda zai ishe ta a bokiti tace tayi wankan bari ta haɗa abin ƙari, Indomi ta dafa masu sai ruwan shayi,sai da ta karya sannan ta shiga wanka, Ta fito ta na saka kaya ta ji maganar shi da Aisha wacce tuni ta shirya cikin riga da wondo da aka kawo mata tsaraba, Kallon agogo ta kuma yi,goma da minti sha-biyar, Jin shigowar shi ne yasa ta juyo tana kallon shi, Takowa yake gabanta "Sumy na kin yi kyau" "Na gode' Mayafin ta dake gefe ya ɗauka ya mika mata" Muje " "Kai ba zaka shirya bane" Ta faɗa tana kallon shi da wannan shigar nashi da ta tsana. Washe baki yayi"ai ni a shirye nake" Turo baki tayi"a haka" Shima ƙara kallon kanshi yayi"eh,kinsan dazu na saka kayan nan kuma basu yi komai ba" Ƙara turo baki tayi tana yin wurgi da gyalen hannun ta kan gado"to ni dai in dai wannan kayan zaka saka ba zanje da kai ba sai ka dawo " "To yanzun ya kike son in yi,ok to bari na canja" Har ya juya sai kuma ta dakatar dashi da sauri,durowan kayanta ta buɗe ta dauko jakkan ta mika mashi, Amsa yayi"na menene wannan " "Kayan dana tsiyo maka ne a England da muka ke shopping," Amsa yayi ya buɗe jakkan yana dubawa,baimasan sanda ya shiga sake murmushi ba,"na gode Sumy" Ɗaukar jakkan yayi ya fita dashi,bai jima ba sai gashi ya shigo cikin shigar bakin wando da da riga Sky Blue ba laifi yayi kyau, Yana shigowa ya shiga washe baki"kinga Sumy nayi kyau ko? Nuna mashi kujerar madubi tayi"zauna anan" Zama yayi ta dawo gaban shi ta tsaya,"me zaki yi Sumy Baby? Bata bashi amsa ba ta dauko karamin Kum da mayukan kai,ta shiga shafa mashi a suman shi da duk ya naɗe,hand dryer da ta siyo ta dauko ta jona,nan ta shiga aikin gyara mashi suma,kafin kace me sai gashi suman ya kwanta a kanshi har daukar ido yake tsabar yanda yaji kyara, "Kanada sheba? Cikin jin daɗi yace" Eh bara na dauko maki " Da sauri ya koma dakin shi ya dauko mata,amma Digital ne,dan haka a hankali tayi amfani dashi ta kyara mashi fuska tas,duk gashin da ke fuskar a yamutse ta fitar dashi,sai dan sajen data bar mashi, Kallon fuskar shi yake a madubi tamkar yanda take yi,ta cikin madubin yake sakar mata murmushi"Sumy Baby kinga yanda nayi kyau sosai ko? Na gode Allah ta maki Albarka," "Amin"ta amsa tana yaba yanda kyara ke kyara mutum,ɗan wani tunani ne ya faɗo mata,nan take ta sake murmushi,wato ganin yanda fatan shi ke a murje saboda Jauro baya cin ƙazamin abinci,zai iya kashe ma kanshi ko nawa ne dan ya koshi,sai dai ko Mai na shafa bata tunanin yana da na Arziki,dan haka sai ta saka ya koma shafa Mai mai tsada ta yanda cikin kankanin lokaci zai washe ya dawo dan gayu (A zuciya ni ma nace Allah yasa dai kar a siya mashi Man bilicin) "Ni dai ka tashi mu tafi tunda an gama kaga sha ɗaya har tayi" Mikewa yayi ya dauko mata kyalen da ta yi wurgi dashi ya mika mata "mu je ko" Tare suka fito sannan ta kashe kayan Kallo suka fita, Shi ke jan motar tana zaune a gefen shi,sai Aisha dake baya, Sunyi tafiya mai nisa a cikin gari kafin tace"ni kan kamar hanyar gidan ka ji " "Ashe kina gane wuri" Zaro ido tayi"ba dai kashin kajin zaka kai ni na kwashe ba? Dariya yayi yana dauke hanyar wurin in da taga sign Board an rubuta EL WAZIR,(Littafi na mai zuwa) Cikin unguwar suka shiga,tun daga bakin layin take kallon wani irin makeken katanga wanda sai tafiya suke da mota amma basu kai ƙarshen shi ba, Nuna mashi katangar tayi"nan ina ne,ko kamfani ne? "A'a gida ne" Cikin mamaki tace "gida kuma,amma naga kamar yayi rabin unguwar ai,yanzun akwai mutane ciki? " A'a mutum ɗaya ne ina ga a ciki" Mamakin ta ya ƙara karuwa,tana juyawa baya dan kara kallon katangar da suka bari"duk wannan katon gidan,to ai wannan yaci rabin unguwar,to waye a ciki? Kai tsaye ya bata amsa da "EL WAZIR" Shiru tayi tana maimaita sunan a zuciyar ta,tana kuma mamaki,jin yayi parking a ƙofar wani gida ne yasa ta ɗaga kai tana kallon ƙofar madaidaicin gidan, "Gidan abokin aiki na ne,matarshi ta haihu ku shiga ku mata barka " Mika mata wani babban leda yayi"wannan ki bata,da kin ce mata matar Jauro ce ke zata gane" "Ok " Ta faɗa suna fitowa daga cikin motar, Kamar yanda ya faɗa haka tayi,ai kuwa matar ma ba wata babba bace,ta kuma ji daɗi sosai,gata da fara'a, "Kiyi haƙuri bamu samu halartar bikin ku ba,lokacin ina fama da ciki" "A'a babu damuwa nasan wata rana ke ma zaki zo" Cikin sakin fuska tace"insha Allah " Wata yar budurwa ce ta shigo gidan ta zauna tana sauke numfashi, "Lafiya Zainab? Hajara ta tambaya,wato mai Jego, " Ke dai bari na gama sauke numfashi,wallahi Aunty Hajara Salmanu bai da hankali, kin San Me ya faru " "A'a sai kin faɗa " "Katangar gidan EL WAZIR ya je ya jingina dashi yana ɗaukar hoto,na faɗa mashi sunan shi gawa,domin ba'a taba koda katangar gidan WAZIR mutum ya kwana lafiya,gani yake kamar wasa nake yi,Allah kaɗai yasan iya adadin mutanen da suka mutu" Zaro ido tayi"shikan wani tsautsayi ya aike shi,Allah yasa yana da sauran shan ruwa" Kallon su tayi"waye EL WAZIR ,bani labarin shi" "Ke rufa ma kanki Asiri,domin irin su ba'a bada labarin su,hakan hatsari ne amma dai mutum ɗaya ce zata iya sanar dake waye shi" "Wacece ita" "JIDDARH UMAR" "Ina zan same ta dan gaskiya so nake na San komai" "Ki bari duk randa nazo har gidanta zan kai ki" "Kafin nan dan Allah ina da tambaya,shin wannan EL WAZIR din hala tsoho ne" Tare suka haɗa baki wurin bata amsa"Yaro ne ƙaramin da bai wuce shekara Ishirin ba" Wannan karon mamakin ta ya kasa boyuwa,sai dai kafin ta kara sako masu wata tambayar,sai ga mikin Aunty Hajara ya shigo yana faɗin "Amarya wai ki fito ku tafi Jauro na jira" Murmushin dole ta kakalo domin Allah ya gani taso ta ƙara jin wani abin, Ya ta iya,haka dai tai masu sallamah ta shiga mota suka tafi, Sai dai wannan karon ta wata hanyar yabi cikin unguwar sai gasu sun bullo bakin titi ba tare da sun bi ta wurin gidan EL WAZIR ba(coming soon), Sunyi tafiya sosai kafin ta gane inda suka dosa,bata dai ce mashi komai ba har aka buɗe masu Get suka shiga, Sai dai maimakon taga sun tsaya wurin rannan sai gani tayi sunyi tafiya mai nisa daga wurin kafin ta hango wani Flat,nan ma suka wuce sannan suka isa wurin wani lambu mai matukar kyau, Parking yayi ya fito sannan ya buɗe mata ita ma ta fito ita da Aisha, Rayawa take a ranta,in dai har aiki ya kawota tayi ai kuwa sai ta shuka mashi rashin mutumci,sai dai kuma wurin ya burge ta sosai,ga iska mai daɗi dake kadawa............ *🍂JAURO🍂* (MAI ANGUWA) Story & Writing By JIDDARH UMAR 🌟🌙🌙🌙🌙🌙🌙🌟 *🌙✨MOONLIGHT WRITER'S ASSOCIATION🌙✨* https://m.facebook.com/Moonlight-writers-association-109698351308376/ *'''We are the moonlight writers we shine all over the world.''🌍'* ✍️✍️ بِسم الله الرحمن الرحيم ~~~~~~~💞💞~~~~~~~ *Ban yarda wani ko wata su saka min littafi a shafin su ko su mai da min littafi Audio ba tare da izini na ba* *46* *Wannan littafin nawa mai suna a sama na mai da shi na kuɗi,tare da Yar Tsanar Zinare,wanda yake son guda ɗaya dari uku 300,guda biyu 500 dari biyar, Hauwa Umar,Zenith Bank,2284905309,sai shaidar biyi ta wannan number 08141644865* Ganin sun tsaya kalle_kalle ne yasa yace"mu je " Da sauri ta bi bayan shi,har cikin lambun in da ta hango wasu tsofaffin Fulani zaune suna hutawa saman Dardumai, Sallamah tai masu tamkar yanda shima ya yi,ta cire takalmi ganin ya cire, Murmushi duk suke sakar masu kafin daya daga su yace"Ƴata Bismillah kara so nan ku zauna, Karasawa suka yi ta zauna kusa da Jauro,cikin natsuwa ta gaida su,suna amsawa, Wani mutumin ne ya zo ya gaida su,kafin Jauro ya juyo wurin Aisha "zaki sha daran shanu? Ya tambaye ta, Da sauri ta gyaɗa kai, Murmushi yayi ya juyo kan mutumin dake tsaye" Muntari kai ta ka tatsar mata madara mai zafi" "To angama" Hannu ya mika ma Aisha "kanwata taso mu je" Tashi ta yi ta bi shi, Kara cewa yayi"ka zagaya da ita in akwai abinda take buƙata ka bata " Nan ma amsa mashi tayi da angama. Hira suke janta dashi sama sama,suna kuma saka ma rayuwarta Albarka wanda hakan ba karamin daɗi yake mata ba, Jauro ne yace masu zasu je su ɗan zazzaga kafin su tafi, Dan haka sallamah ya masu tare da faɗa masu sai zuwa yamma in ya dawo, Suna fitowa lambun tace"iyayen ka na da kirki" Murmushi yayi"na sani" Tabe baki tayi,"to ina kuma zamu,naga sai tafiya muke" "Siyar dake zan je yi" Kallon shi tayi"ka taɓa ganin in da mutum ya saida kanshi " "Kamar ya" "Bar shi kawai" Murmushi yayi domin ya fahimci me take nufi, "La kalli shanaye da yawa" "Mu je ki gani" Cikin zumudi tabi bayan shi suka je wurin,sai dai dan nisa kaɗan da wurin suka tsaya tana kallon su,manya da yara, Ba tare data kalle shi ba tace"Shanayen nan sun kai guda nawa? "Suna da yawa" "Ina son na san wanda nake Aure,shin zaka bani damar haka? Wannan karon juyowa yayi yana fuskantar ta,sai dai ita bata kalli shi ba,hankalin ta ya kan dabbobin da ke gabanta. " Tunda har kin buƙata me zai hana " "Wannan gidan gonan na waye? " Nawa ne" "Waɗannan Dabbobin fa? " Duk wani abinda kika fara gani tun daga bakin Get har karshen katangar gidan mallakina ne" "Idan har kanada wannan Arzikin me yasa ka aure ni a haka,na tabbatar da waɗanda suka baka aure na basu san komai ba dangane da kai,me yasa ka ɓoye masu ni ma kuma ka ɓoye min"ta faɗa tana juyowa gabaɗaya suna fuskantar juna. "Iyayen ki basu buƙaci su da susan haka ba,mu je ki ƙarasa ganin wurin" Bin bayan shi tayi suka fara takawa yana nuna mata ɓangare_ɓangare na gidan gonan. Sakawa yayi aka cire masu ƙaton kifi guda daya sai kayan miya da aka zuba masu a bayan mota,harda kwai kiret biyu, Kallon shi tayi"ina buƙatar madara" Shima sakawa yayi aka kawo cikin ƙaramin jarka. Mota suka shiga suka bar gidan gonan da A'isha wacce ki ji kamar kar a wuce, saboda kayan daɗin da ta ci, Tunda suka fito bata ce mashi komai ba har suka yi nisa, Ɗan kallon ta yayi"ki yi haƙuri idan har faɗa maki da banyi ba ranki ya baci, A lokacin gani nike baki shirya sanin ko ni waye ba, Gobe idan Allah ya kaimu zamu je ƙauyen mu ki gaida iyaye na" "Ni kuma nawa iyayen yaushe zanje na gaida su" "Naga wasu Amaren suna kaiwa wata hudu ko shida kafin su je gaida iyaye" Cikin jin haushi tace"ba dai ni ba,ƙila gara su suna da wayar da ako yaushe suke ra'ayin jin muryan iyayen su sana iya ji,amma ni ko waya nace a ara min ko kallo na ba'a yi, dan haka karka fara wannan tunanin " Bai bata amsa ba dai yaci gaba da tukin shi, Gani tayi ya shiga Obasonjo complex,"ina zuwa"ya faɗa bayan yayi parking a cikin, Bai wani jima ba sai gashi ya dawo hannun shi rike da leda,yana shigowa ajiye mata ledan yayi saman cinyan ta"ina fatan zaki zauna har na wata huɗu kafin ki je gida,tunda yanzun kin samu abin jin muryar su"ya faɗa yana ta da mota, Ciro kwalin dake cikin ledar tayi, Aikuwa kwalin yawa ne wanda taga samfarin IPhone ne,gashi an saka Iphone 12, Kallon shi tayi ta kuma kallon wayar,"nawa ne? Ta tambaye shi cikin mamaki. "Ummm" Cikin sauri ta dauka ta maida mashi saman cinyar shi "to ni dai bana so in dan kaki bari na naje gida ne har na tsayin wata shida wallahi ba ni so" Bai kula ta ba yaci gaba da tukin shi har suka isa gida,wanda ba karamin kule ta yayi ba,dan haka yana yin parking ko tsayawa ya buɗe mata bata yi ba ta buɗe murfin motar ta fita ba tare data kulle mashi motar ba. Aisha ce ta taya shi suka kwashe kayan dake bayan boot zuwa kicin, Sannan ya kunna mata kallo, Dakin ta ya shiga in da ya same ta kwance saman gado tana faman rusa kuka, Girgiza kai yayi ya ƙarasa in da take,kiran sunan ta ya shiga yi amma ko kula shi bata yi ba, Zama yayi a bakin gadon yana ajiye kwalin wayar dake hannun shi, "Amma ke kika faɗa da bakin ki" Filon dake gefenta tawurga mashi. Cabewa yayi,yana murmushi "to shikenan na fahimta," Mikewa tsaye yayi zai tafi"karki manta gobea da wuri zamu fita " Cikin kuka tace"wallahi ba inda zan je,tunda ba zaka kai ni gida ba" "Iyayen nawa ne ba zaki gai dawa ba? Kin kula shi tayi ta ci gaba da kukan ta, Ƙara zama yayi" Shikenan naji zaki ki gai da su" Wani zabura da tayi ta Mike shi kanshi sai da ya matsa baya, Nan take ta shiga share hawaye ta tas tamkar ba ita ta gama kuka ba,"da gaske,yaushe zan je? Ta tambaya cikin murmushi. Kallon ta yake cikin mamaki,"nan da wata biyu " Kafin ya gama rufe baki tuni ta kara fashewa da kuka wanda yafi nada ƙarfi dan wannan karon har darda filollukan dake kan gado ta shiga jifa dashi,"wallahi ban yar da ba,ni dai ban yarda ba wata biyu yayi nisa" Da gangan ta shiga shureshi da ƙafa, har sai da ya zame daga kan gadon, Kallon ta take tamkar wata me Aljannu "kin ga ya isa karki ji ma kanki,ki bari idan zan je mai da Aisha sai mu je tare" Bai ga sanda ta tashi ba sai jinta da yayi a jikin shi makale tana dariya,"na gode sosai Jauro,na gode " Shiru yayi yana sauraron bugun zuciyar shi,so yake ya tabbatar da yanda yake ji ko yanda zai ji, Sai dai zafin jikin da yake ji a cikin kashi dari kashi arba'in ne yayi saura,dan haka ba sosai zafin ke ratsa shi ba, Cikin tsananin farin ciki ya cire ta a jikin shi,dan baya buƙatar ta san meke faruwa, "Ɗaga ni ya isa haka,kafin na canja ra'ayi" Da sauri ta sake shi tana dariya, Daukar kwalin wayar yayi zai wuce dashi, Cikin sauri ta rike ledar "ina kuma zaka je min da waya? " Cewa fa kika yi baki so" "Da yaushe kuma na ce haka,kaga bani waya ta" Ta faɗa tana fizge ledan, Girgiza kai yayi kawai yana barin ɗakin yana tunanin irin tarbar da zasu samu a ƙauye,Allah dai yasa kar ta jawo mai abin magana, Dan dazu suna gidan barka ake sanar dashi cewa sun sako Baffa Sanda amma yana Asibiti shima,dan haka gode can zasu fara zuwa kafin su tafi ƙauye...... *🍂JAURO🍂* (MAI ANGUWA) Story & Writing By JIDDARH UMAR 🌟🌙🌙🌙🌙🌙🌙🌟 *🌙✨MOONLIGHT WRITER'S ASSOCIATION🌙✨* https://m.facebook.com/Moonlight-writers-association-109698351308376/ *'''We are the moonlight writers we shine all over the world.''🌍'* ✍️✍️ بِسم الله الرحمن الرحيم ~~~~~~~💞💞~~~~~~~ *Ban yarda wani ko wata su saka min littafi a shafin su ko su mai da min littafi Audio ba tare da izini na ba* *47* *Wannan littafin nawa mai suna a sama na mai da shi na kuɗi,tare da Yar Tsanar Zinare,wanda yake son guda ɗaya dari uku 300,guda biyu 500 dari biyar, Hauwa Umar,Zenith Bank,2284905309,sai shaidar biyi ta wannan number 08141644865* Tunda taga ya bar dakin cikin farin ciki ta faɗa kan gado tana rungume wayar,buɗewa tayi a cikin kwalin sannan ta saka a caji, Ganin lokacin sallah yayi ne yasa tace Aisha ta tashi suyi sallah,sai da suka idar sannan ta koma kicin,abubuwan da suka dawo dashi ta adana ko wanne in da ya kamata,shi kuma madaran shanun,juyewa tayi a wankakken tukunya sannan ta daura a Gas,tana tsaye har ya tafasa daya sannan ta sauke,ta koma daki,sai bayan mintuna sha-biyar sannan ta dawo ta juye a wani karamin roban fenti sannan ta wanke tukunyar, Allah_Allah take wayar yayi caji ta saka number Mama da Aunty Amina ta kirata,she can wait to call them with her new phone,ai kuwa Mama ta shiga uku da kira. Da daddare miyan farfesun kifin da suka dawo dashi tayi suka ci da tuwon shinkafa, Washegari kamar yanda ya tsara ƙarfe goma suka nufe Asibitin IBB in da a can Baffa Sanda ke karɓar treatment, Adaidaita ya zo har kofar gida ya dauke su zuwa Asibitin, Suna fitowa a Adaidaita ya amsa basket din abincin dake hannun ta"Idan mun shiga ki gaida kowa cikin girmamawa" Baki buɗe take kallon shi"kana nufin banda tarbiya? "Nifa ba haka nake nufi ba,kawai dai b... Cikin jin haushi ta fisgi hannun Aisha" Kaje kawai na fasa shiga gidan mu zan koma Mama ta ƙara ban wani tarbiyya " Da sauri ya ajiye basket din dake hannun shi ya riƙo nata hannun,kallon Aisha dake kallon su tayi,yana lumshe ido,sam baya son suna nuna hali a gaban wannan yarinyar ƙarama,saboda yaran yanzun baki gare su, Jawota gaban shi yayi"come on Sumy,why do you always want to take a fight with me,i know you know that is not what I mean,please not now ok" Kara hasala tayi "ohh is that what you support to say,wato ni ce mai son tsokanar ka faɗa bancin ka kirani da mara tarbiyya ko,shi ne zaka faɗi haƙa"ta karasa faɗa tana shirin saka kuka Dafa goshen shi yayi yana lumshe ido,shi ya zai yi da rigimar wannan yarinyar,shi kwata_kwata yanda ta ɗauki lamarin ba haka yake nufi, Jawota jikin shi yayi ya rungume tunda bashi da option kafin ta tara mai mutane, Shafa bayanta ya shiga yi"ok I am sorry that is my bad,I'm not to say that to Queen Sumy,kuma ni nasan kina da tarbiyya sosai,idan da ba dan tarbiyyar ki ba ai ba zan yarda na aure mace wacce ba irin ki ba," Kokarin kwace kanta take yi ya kara rungume ta "in baki ce kin hakura ba bazan sake ki ba" Jin ya ce haka ga kuma Aisha a tsaye yasa da sauri tace"na hakura sake ni"dan tasan shi babu ruwan shi ba kunya ne dashi ba, Sake ta yayi"are we good? Hararan shi tayi kafin ta bashi amsa sun ji daga bayansu ana daɗin "Jauro kai ne? Duk juyawa su kayi suna kallon matar wanda kallo daya zaka mata ka shaida zamowarta cikakkiyar Bafulatana, Murmushi ya sake yana karasawa in da take tsaye daga dukkan Alamu wucewa za tayi," Goggo Halira ni ne,ba dai tafiya za ki yi ba? Itama murmushi ta saki"wallahi tafiya zanyi dan tun da safe nake nan," Karasowa in da suke tsaye tayi,cikin girmamawa ta duka ta gaida matar data ji ya kira da goggo, Amsawa tayi tana kallon kyakkyawan yarinyar "wannan kuma wacece,ƴar nan ki yi hakuri ban gane ki ba" Dariya yayi"to Goggo ai yarki ce" Kallon shi tayi,ganin yana mata dariya yasa ta gane"Oh Oh Oh Amarya ce ashe"daga ta tayi daga duken da take, "Kinga kyale wannan dan nawa taso mu koma ciki,da tafiya zan yi amma na fasa," Ta fada tana jan hannun ta suka yi cikin Asibitin. Wani daki ne suka shiga wanda a kalla marasa lafiya shida ne a ciki, Wanda suka tsaya shi daga Dattijon dake kwance yana barci sai wata mata wacce daga dukkan alamu ƙila matar shi ce, "Kande ga matar Jauro ta zo duba ku" Kallon ta matar ke yi daga sama har kasa tamkar yanda ita ma take kallon matar,gaida ita tayi da me jiki, A takaice ce ta amsa tana jin haka kawai wani abu na tsaya mata a makoshi,yanzun duk wannan cikakkiyar kuma hadaddiya matar Jauro ne,to a ina ya samo ta,kalle ta jajir da ita,amma idan ta tuna kalan matar su Dottiya da Yabbale sai ta ji abu ya soke ta a zuciya,gasu kazamai,ga shi haihuwa biyu kawai yanda kasan tsofaffin, "Bikin da aka kasa jira mu dawo ayi damu,kila tunani yake ba zamu dawo ba" "Ki yi haƙuri innan Yabbale,Allah ne ya kawo lokacin a gaggauce wanda ba wanda ya isa ya dakatar shi yasa" "Ke kuwa abunda an ka riga an ka yi,yanzun dai Albarka kawai ya rage ki saka masu sai ki bi su addu'a" Cewar Goggo Halira. Kamar ba zata ce komai ba sai kuma tace"Allah ya bada zaman lafiya " Da Amin suka amsa,sannan ya ajiye mata Basket din da suka zo dashi, Goggo Halira ce ta fara yin gaba,sai shi dake bayan ta, Ji tayi matar tace "Allah yasa ma ka kasa rike ta tunda kaje ka dauko abunda yafi ƙarfi ka" Duk juyowa sukayi suna kallon ta, "Me yasa zaki ce haka Kande bayan yanzun kika gama saka Albarka" Cewar Halira da harshen fullanci wanda ita ma dashi ta yi maganar, Shiru yayi kawai yana kallon ta ya rasa me ya tsare ma waɗannan mutanen har abada basu taba bin shi da Alkhairi, "Ai ba karya na faɗa ba,in banda rigima ba sai ya ɗauka a kauye kamar yanda sauran yan uwan shi suka yi ba,in Allah ya yarda ya ɗaukar ma kanshi bala'in da zai halaka shi tunda karya ya saka a gaba" "Kamar yanda kika ambaci Allah,to insha Allah ba zai taɓa ganin bala'i ba,aure na dashi kuma sai ya kasance mai Alkhairi da abin Alfahari,ƴan bakin ciki sai dai su mutu" Ta faɗa cikin harshen Fullanci wanda gabaɗayan su sai da suka jijjiga jin abinda ta faɗa, Daga ita wacce ta faɗa har goggo Halira mamaki da kunya ce ta kamasu,har balle Kande wacce bata taɓa tsammanin yarinyar najin yare ba,sannan bata taba tunanin zata maida mata da amsa ba, Yayin da shi kuma yake tunanin dama tana jin Fullanci bai taɓa sani ba. Cikin kwanciyar hankali take takawa har tabar dakin riƙe da hannu Aisha, Kallon ta goggo Halira tayi "yau dai kam kin ji kunya Kande" Juyawa tayi tabi bayan su,ganin bata gansu bane yasa ta zagaya ta baya in da sauran ƴan uwa ke zaune, Yana tsaye ita kuma tana zaune saman tabarma ita da Aisha kusa da Goggo Badejo,dake mashi tsiya akan bai kaimata Amarya gidan ta ba,haƙuri yake bata akan sunanan zuwa su gaida ita. Matar Dotti ce tace"ai kuwa Jauro ta fika kyau,a ina ka samo ta" Duk dariya suka yi, Bakari shida Shafi'u yaran Baffa Bube ne suka iso wurin, "Wai me yasa ku har yanzun ba za ku yi hankali ba,kun zo kun same mutane amma babu sallamah balle gaisuwa kun zo kun ma mutane tsaye a kai kamar a kwai tsaranku anan,"cewar Goggo Halira wacce isowar ta wurin kenan. Cikin rashin kunya Shafi'u yace" Saboda an tsane mu shi yasa ba aso mu zo,to wucewa zamu yi ma," Duka goggo badejo ta kai mashi a baki ai kuwa cikin sa'a ta same shi da kyau "shege me bakin hali,mu zaka ma rashin kunya,to ko Uwar taka ba ta isa muna wuri ta shigo mana haka ba, shegu sun tsotse nonon tsiya,in kun ga dama karku kara zuwa nan,su kuma wadancen yannin naku ba dai sun ƙi zuwa ba,ina nan zuwa har gida na same su,sai sun nuna min wanda yake ɗaure masu gindi" Sun san halin goggo badejo da faɗan tsiya dan haka ba tare da sunce komai ba suka bar Asibitin, "Goggo zamu tafi Ruga dan ina son mu je har gidan Malam liman" "Gaskiya kam ya kamata ku je,ni ma da naso na shiga ƙauye amma sai dai zuwa gode" Mikewa tayi suka masu sallamah sannan suka fito Asibitin, A bakin Get ya kuma tare masu abin hawa sannan ya faɗa mashi inda zasu, Cewa mai adaidaitan yayi "ku ba da dubu daya" Bai masan sanda ya harari mutumin ba"in da ake zuwa dari uku shine zaka ce dubu daya? "To ai faɗa nayi in bai maka ba sai ka faɗi iya yanda zaka iya biya" "Na maka kama da wanda zai tsaya ciniki,ko kuma kaga Alama ba tafiya zanyi ba" "To ku bada dari biyar" "In baka zuwa...... Kafin ya karasa har sun shige cikin Adaidaitan" Muje Malam " Ai kuwa jan mashin din mutumin yayi yana ƙoƙari wucewa, "Kai kai ina zaka wuce min da mata" Ya faɗa da ƙarfi, "Malam karka tsaya" Ganin da gaske wucewa yake yasa da gudu ya bi su ya dale cikin Adaidaitan yana sauke numfashi, "Kai mahaukacin ina ne,tsaya_tsaya mun fasa tafiyar,guduwa zaka min da mata? Ji yayi tace" Malam cigaba da tafiya " Kallon ta yayi"guduwa da zai yi dake fa? "Ni nace ya tafi" "To why? " Saboda naga kamar baka shirya tafiya ba" "To kin san wurin ne? " Ai kai kasan wurin " "Dafe kai yayi,Oh Sumy,ni dai to dari uku zan ba shi" "Dari biyar zaka bashi" "A'a ba zan biya ɗari biyar ba" Juyowa tayi tana fuskantar shi "dubu daya zaka bashi" Zaro ido yayi"me yasa zan bashi har dubu daya? "Saboda kanada shi" Nuna mai Adaidaitan yayi wanda yake ta kwasan dariya, "Sumy this is not fear" Ajiyar zuciya ta sauke tana shafa kumatun shi"karka damu nasan kafi karfin haka" "Amma.... " Shiiiiiii"ta faɗa tana daura ɗan yatsarta saman labban shi, Shiru yayi ya kauda kai yana turo baki,wanda hakan ba karamin dariya ya basu ba,ai kuwa darawa suka shiga yi ita da Aisha,dan yanda kasan wani auta haka yayi. Juyowa yayi kuma yana kallon ta kafin ya kira sunan ta"Sumy" Juyowa tayi batare data amsa ba. "Dama kina jin fullanci baki faɗa min ba" "Baka tambaya ba ne" Shiru yayi wato ramawa tayi,"ok bani labari" "Akan me" "Akan taya kike jin fullanci bayan nasan Baba Bahaushe ne how come" "Wacce ta haifi Baba Fulani ne sosai,ƴar Katsina,mun zauna tare da ita har Allah ya mata rasuwa lokacin ina SIS 2 a secondary School,kuma fullanci take mana,dan haka duk muna ji" "Wow,that is impressive,,to akwai kuma abinda ya kamata na sani ne" "Kamar me? " Kamar komai,dan bana son mata ta tana ɓoye min wani abu" Gani yayi tayi shiru ta maida hankali kan labaran da ake yi a gidan rediyo,in da mai bayanin ke nasar da cigiyar masu ra'ayin koyarwa a makaranta Secondary,aka kuma fade in da Venue din yake da kuma lokacin da za'ayi gwaji dan tantancewa. Gabaɗaya dawo da hankalin ta kanshi tayi ta riƙe hannun shi,"kace in akwai abinda ya kamata ka sani na sanar da kai saboda ni matar ka ce ko? Jinjina kai yayi, "Ka amince ciki harda buri na? Nan ma jinjina mata kai yayi. " A rayuwata bani da buri da ya wuce na samu aikin koyarwa domin na taimakama mahaifiyata,tasha wahala da ɗawainiya dani har sanda taga na samu abinda nake so, Ni kuma gani nake ta hanyar yin aiki da kuma taimaka mata ne kaɗai zan iya saka mata da kuma nuna mata bata yi asaran kudin banza ba, Dan Allah ka taimakamin na cika buri na "ta ƙarasa faɗa idanunta nayin raurau da hawaye,yayin da gabanda ke faduwa na tsoron abinda zai fito bakin shi. Shiru yayi na dan wani lokaci,yayin da ke jin yanda take ƙara matse hannun shi a cikin nata, " Ki bari in mun je gida sai muyi magana " Lumshe ido tayi tana jin tamkar ta shiga zuciyar shi ta ji me zai ce. Dan murmushi mai Adaidaitan yayi,domin ba karamin burge shi suka yi ba...... *🍂JAURO🍂* (MAI ANGUWA) Story & Writing By JIDDARH UMAR 🌟🌙🌙🌙🌙🌙🌙🌟 *🌙✨MOONLIGHT WRITER'S ASSOCIATION🌙✨* https://m.facebook.com/Moonlight-writers-association-109698351308376/ *'''We are the moonlight writers we shine all over the world.''🌍'* ✍️✍️ بِسم الله الرحمن الرحيم ~~~~~~~💞💞~~~~~~~ *Ban yarda wani ko wata su saka min littafi a shafin su ko su mai da min littafi Audio ba tare da izini na ba* *48* *Wannan littafin nawa mai suna a sama na mai da shi na kuɗi,tare da Yar Tsanar Zinare,wanda yake son guda ɗaya dari uku 300,guda biyu 500 dari biyar, Hauwa Umar,Zenith Bank,2284905309,sai shaidar biyi ta wannan number 08141644865* Tunda suka shiga Rugar take kalle_kalle yanda kowa ke gudanar da abinda ke gaban shi, A da ta dauka ko ƙaramin ƙauye ne,amma ganin yanda gidaje ya cika ko'ina yasa ta gane ƙauyen na da yawa, Abakin wani masallaci yasa suka sauka, sannan suka shiga gidan dake jikin Masallacin, Abakin zaure ya haɗu da Moha wanda dama ya sanar dashi zuwan su, Rungume juna suka yi suna dariya,kafin ya juyo in da take tsaye tana kallon su, "Amaryar mu sannu da zuwa Ruga" Ya faɗa da Hausar shi wanda fullanci ya kwace, Cikin sakin fuska ta gaida shi, Shiya masu jagora har dakin bakin da Malam Liman ke zaune, Ai kuwa ba karamin daɗi tsohon yaji ba,ya kuma saka masu Albarka sosai,sannan yace Jauro ya kai ta cikin gida ta gaida iyaye mata, Saida suka gaida matan Malam Liman sannan suka shiga dakin Uwargidan Moha,wanda matan shi biyu, Basu jima ba kuma shida Moha suka fita suka bar ta nan suna hira,dan matan ba su da matsala ga sakin fuska, Abinci kuwa da nama duk ci irin na ta sai da tabarshi,dan ita in dai wurin ci ne ba ruwanta da baƙunta, Daya daga cikin yaran gidan ne ya shigo wai ta fito in ji Jauro, Matan gidan ne suka rakota har ƙofar gida sukai mata sallamah, A ƙofar gida ta same shi tsaye shida Abokin shi,yana ganin ta ya taso,"me kika ci haka naga bakin ki da manja" "Da gaske? " Ummm"ya faɗa yana jinjina kai, Hannu ta saka ta shiga goge baki,tana kallon shi "ya fita" "Me kenan? " Manjan " "A ina? Ya tambaye ta, " Amma yanzun kai kace akwai manja a baki na " "Ni da yaushe na faɗa,ni banga komai ba a bakin ki" Duka ta kai mai a kafaɗa,da sauri ya goce yana dariya, Hararanshi tayi tana ƙara ma tafiyar ta sauri ta bar shi a baya yana dariya. Ganin tana ƙoƙarin bin hanyar da bashi bane yasa da sauri yace"malama ba nan zaki bi ba," Tsayawa tayi"to ni dai dan Allah kazo kai mana jagora,ni in da ma nasan gidan da ba zan ma jira ka ba" Karasowa yayi inda take ya riƙe mata hannu,"tanan ne hanyar "ya faɗa yana bi da ita ta wata hanyar, A hankali suke ta ratsa ta cikin gidajen Fulani da kuma gonaki,har suka iso ƙofar wani gida mai babban iccen Darbejiya, Kallon ta yayi ya kalli zauren gidan dake gabansu,juyo da ita gaban shi tayi" Kin ga wannan gidan? Ya faɗa yana nuna mata, "Anan nan iyaye na suka rayu,anan kuma suka mutu,anan na rayu kuma na tashi,ina girmama wannan gidan,sai dai mutanen dake rayuwa a cikin ba kamar yadda kike tunanin suke ba,ina fata duk tarbar da kika samu ba zaki yi korafi ba,kuma duk abinda kika ji zaki toshe kunnen ki" Jikin ta ne yayi sanyi,domin tunda take dashi bata taba tambayar shi yaya iyayen shi suke ba,ko da kuwa tace ya gaida mahaifiyarsa,cikin sanyin murya tace"to ina mahaifinka? Murmushi yayi mai ciyo,yana tuna irin mutuwar da mahifiyarsa tayi cikin jini da a zaban nakuda,da irin niman taimakon da ya rinka yi a wurin jama'ar gidan amma aka rasa wacce zata taso ta leka koda a wani hali take,har ta rasu jini ya sandare,wannan yana daya daga cikin bakin cikin da ya karasa mahaifinsa,"ya rasu bayan sati biyu da rasuwar Inna ta" Bata masan sanda ta saki hannun Aisha ta rungume shi ba,"I am Sorry! I am sorry for not asking you about them" Shafa bayanta yayi yana murmushi "kar wani ya fito ya ganmu" Ƙara rungume shi tayi,"don't worry I will take care of you " "Keda kike min rashin kunya ta yaya zaki kula da ni? Kafin ta bashi amsa ne suka ji daga bayan su tana salati tare da tafa hannu" Hande min boni,yau me zan gani,yanzun Jauro Karuwancin naka har ya kai kazo da Mace ƙauye ka rungume ta a tsakiyar gari" Duk juyowa suka yi suna kallon me managa, Daga bayan shi kuma suka ji ance" meke faruwa nake jin salati" Ƙara cewa yayi"Baffa Jauro ne yazo da ƙaruwa har gida suna rungume juya babu kunya" Kafin tsohon yayi magana cikin bacin rai yace"Ɗan Fodio ka iya bakin ka,yanzun in banda rashin da'a da rashin sanin ciyon kai matar tawa zaka kira da ƙaruwa? Duk sai lokacin suke kare ma yarinyar da ya kira da matar shi kallo, Cikin kishi da bakin ciki yace"ko dai menene naka ita ai wannan karuwanci ne,ta yaya a ƙofar gidan mu,gamu da ƙananan yara zaku zo kuna wani rungume juna,in banda yan iska" Idan ranshi yayi dubu ya baci akan kalmar daya jefe matar shi dashi, Kallon Baffa yayi"kana jin abinda yake faɗa " "Yo ni kan Jauro me zan ce mashi,tunda gaskiya ya faɗa,kai ma kasan abinda kuka aikata bai kamata ba" Ya fada yana shigewa cikin wani dakin. "Kaima kasan mu anan ba haka muke ba" "Sai ka faɗa min in da Allah ya haramta,sannan abu na karshe da zan faɗa maka shine,duk randa bakin ka ya ƙara kuskuren kiran matata da karuwa Ɗan Fodio,wallahi! Wallahi ranar sai nasa ƴan sanda sun tafi da kai,sai na saka an shigar min da ƙara Kotu ta yanda zaka faɗa min in da ta dace da wannan sunan,in ba haka ba sai ka yi gidan yari,ka daina tunanin kai ɗan uwa na ne ba zan iya aikata maka hakan ba,tsaf zan cika abinda na faɗa kuma ka kara maimaitawa ka gani"ya faɗa yana mai tabbatar mashi da maganar shi, Tsoro ne ya kama shi,domin yasan duk abinda Jauro yace zai yi to sai ya aikata,dan haka cikin borin kunya yace "ku dai kuka sani" Ya faɗa yana rabawa ta gefen su ya wuce. Juyowa kanta yayi yana ƙoƙarin sai_saita ɓacin ranshi "mu je ciki ki gaida Kaka ta" Jinjina mashi kai kawai tayi,dan ita jikinta ba karamin sanyi yayi ba tun a ƙofa,kafin ma su shiga. Taga dai shiyoyi da yawa a gidan kasancewar yanzun an samu kari harda na Surukai, Daya daga ciki taga sun nufa,sai da yayi sallamah a ƙofar shiyan kusan sau biyar amma ba'a bashi amsa ba,dan haka suka shiga, A zaune a tsakar gida suka iske wata mata tana wanke-wanke,kallo daya tai masu ta kauda kai tana bitar waƙar dake tashi a wayar ta mai kiran Shakidar ka baƙauye, Suma basu ce mata komai ba ya nufe wata ƙofa, Ɗaga labulen dakin yayi yana ƙara yin sallamah, Wata tsohuwa ce sosai ta gani a zaune saman tabarma,sai dai duk da tsufan matar da Alama tana da dan sauran karfin ta, Dago ido tayi ta kalle su"waye a tsaye a kofa? Ta fada da yaren Fullanci, Ganin ya shiga ne yasa suka bishi a baya,wani tabarmar ya dauko ya shinfida suka zauna,"Jauro ne" "Aiyo sai yau ka ga damar zuwa" "Kin ga ni Amarya ta kawo maki ta gaida ke," Ita ma da harshen Fullanci ta gaida ita,tana amsawa cikin sakin fuska, "Ya haƙuri da Ja_irin yaron nan" Murmushi tayi kawai bata ce mata komai ba, "Ɗauko mata fura gashi can ta sha" Daukowa yayi ya kawo mata haɗin Kindirmo lafiyayye, Duk da a koshe take ta san halin tsofaffi,dan haka kaɗan tasha ta mika ma Aisha, Kwala kiran sunan Hajjo ta fara,sai da tayi kira uku wanda suka tabbatar da tana ji kafin ta shigo din babu sallamah,ta tsaya masu a kai"Gani Kaka" "Amma ke kan anyi Tsinanniyar yarinya,bana hanaki shigomin daki babu sallamah ba,? Cikin gungumi ta fita,sai da ta ƙara ɗaukar wani lokaci sannan ta shigo da sallamah, Amsawa suka yi, " Baki ga Jauro bane da matar shi" Kallon su tayi"na gan shi,sai dai ni dama bawai na sanshi sosai bane" Salati ta saka "amma dai kam Hajjo ba kida ɗabi'a,yanzun Jauro ne zaki ce baki sani ba,yaron da har kashi ya wanke maki,ki na matsayin ƴar goggon shi kice baki sanshi ba,ko da kika auri Ɗan Fodio shi ya maki kayan daki duk da bai gari" Kauda kai tayi,domin dama bawai gane shi bane bata yi ba,kawai dai kishin shi take yi,dan ba Ɗan Fodio taso ba,shi taso ta aura amma ya nuna bai da ra'ayin ta,har roko tayi akan a ɗaura masu aure kafin ya dawo zata jira shi,amma kiri_kiri yace baya son ta,sannan yanzun ta ganshi da mata ƴar gayu sannan har ta nuna ta san shi ko kuma ta nuna ta ji daɗin ganin su,Allah ta mata tsari, Katse mata tunani maganar Kaka yayi"to ina ita Uwar taku? Tana nufin Surukarta. "Ta fita suna bata dawo ba" "To ki kawo masu Abinci da ruwa" Da sauri yace"a'a mun koshi " "Ai koda ma zasu ci ya kare dan na yara ne ya rage"ta faɗa tana barin dakin. Baffa Bube ne ya dago labulen dakin," Inna kina ciki ne? "Eh ina ciki,gasu Jauro ma sun zo" "Au basu tafi ba" "Ka gansu ne" Ta faɗa tana tambayar shi, "Eh mun haɗu a zaure" "Jauro naji ance ka dube gidan gona a cin birni" "Eh,Baffa ai yakai shekara biyu,tun lokacin da na faɗa maka sai dai in ka manta ne? " Au ina ce wani ne ka buɗe " "A'a tun wannan ne" "To me zai hana ka dawo dashi ƙauye ai ina ga zai fi,in akwai bisashe,kana iya haɗawa da nawa na maka kiyo tunda mu nan babu matsalar abinci" "Haka ne Baffa" Murmushin nasara yayi,yana zama a bakin ƙofa,maimakon tsaye da yake"yaushe za'a kawo su? "Eh to,bari nayi lissafi,dabbobin gado na yanzun sun kai guda nawa? Nan take ya bata fuska" Bana faɗa maka tsawa ya faɗa masu ba,wasu kuma su ake ta saidawa lokacin kana makaranta ana turama Alhaji Abubakar kudin ya tura maka" Ajiyar zuciya ya sauke"ina ga dai kawai mu bar maganar kiyon nan,dan bana son wani tsawar ta kuma faɗa madu duk da basu wace biyar ba,"ya faɗa mashi haka dan baya son susan abinda ya mallaka. Tsaki ya ja yana mikewa"Inna ni na tafi gona" "To bazaka tsaya ku karasa magana ba? " Kyale shi kawai,sai dai inna dawo"bai jira amsar ta ba ya wuce. Murmurewa yayi"mu zamu tafi kaka sai dai wani lokaci kuma "ya faɗa yana ajiye mata dubu biyu, " Ka dai dinga kawo ta tana shiga dangi " "Insha Allah" Godiya tayi mai tana saka mashi Albarka,sannan suka fito,a bakin ƙofar gidan suka iske Adaidaita wanda yake cike da Doya da kayan miya a bayan but harda kaji guda biyu,duk a gidan Malam Liman me aka basu. Suna shiga mutumin ya ja suka kama hanyar barin Ƙauyen. Lokaci-lokaci takan dan kalle shi,tamkar akwai abinda kecin ran shi..... *🍂JAURO🍂* (MAI ANGUWA) Story & Writing By JIDDARH UMAR 🌟🌙🌙🌙🌙🌙🌙🌟 *🌙✨MOONLIGHT WRITER'S ASSOCIATION🌙✨* https://m.facebook.com/Moonlight-writers-association-109698351308376/ *'''We are the moonlight writers we shine all over the world.''🌍'* ✍️✍️ بِسم الله الرحمن الرحيم ~~~~~~~💞💞~~~~~~~ *Ban yarda wani ko wata su saka min littafi a shafin su ko su mai da min littafi Audio ba tare da izini na ba* *49* *Wannan littafin nawa mai suna a sama na mai da shi na kuɗi,tare da Yar Tsanar Zinare,wanda yake son guda ɗaya dari uku 300,guda biyu 500 dari biyar, Hauwa Umar,Zenith Bank,2284905309,sai shaidar biyi ta wannan number 08141644865* Koda suka isa gida har uku na yamma tayi, Kowa dakin shi ya shige,dan haka wanka ta fara yi sannan tace Aisha ma ta shiga tayi, Riga da siket ta saka,waɗanda suka dame mata jiki, Fitowa tayi ta shiga dakin shi, Zaune yake ya tasa takardu a gaba,sai dai kuma sam hankalin shi baya kan takardun, Alamu ma ya nuna kamar tunda suka dawo ba abinda yayi,har tayi sallamah ta shigo bai sani ba, Zama tayi a gefen shi,ta daura hannun ta saman nashi, Juyowa yayi ya kalle ta yana sauke ajiyar zuciya,"yaushe kika shigo? "Yanzun,nayi sallamah baka amsa ba,tunanin me kake yi? Ta faɗa tana langwabe wuya. Girgiza kai yayi yana dan sakin murmushi," Babu komai,"ya tashi zai bar wurin, Da sauri ta rike hannun shi cikin shagwaba tace"ina zaka muna magana,ba zaka faɗa min ba," "Babu komai da gaske" Bai ankara ba kawai sai ji yayi ta fashe da kuka ta saki hannun shi tare da barin dakin, Da kallo ya bita yana jinjina ma rigima irin nata,to yanzun in banda ita me abun kuka anan, Ba yanda ya iya bin bayan ta yayi, Har ya doshi dakin sai kuma ya dawo baya jin shesshekar kuka daga cikin falon, Tsayawa yayi a tsakiyar falon yana kalle_kallen ta inda zai ganta,dan shi dai sautin ta kawai yake ji amma bai ganta ba, A hankali ya fara bin ta inda sautin ke fitowa,a tsakan kayan kallo da show Glass ya ganta zaune ta haɗe kai da gwuiwa, Tsayawa yayi ya rike Kwankwaso kafin ya tsugunna a gabanta,"Sumy Baby" Kin amsawa tayi ta juya gefe tana ƙara sautin kukan ta, "Why ar you crying? Nan ba kin kula shi tayi, " Ok faɗa min me kike so" Ba tare data dago ba tace"ni ka ƙyale ni,tunda baka dauke ni da muhinmaci ba,i am trying to be nice to you, amma kai baka so" "Duk duniya babu macen da nake bata muhimmanci irin ki,and I know that you are trying to be nice,and I appreciate it" Katse shi tayi"to ni ban gani ba,in da ina da muhimmanci ai dana tambaye ka da ka faɗa min a binda ke damun ka in a nice way,but you confounded me" "Kiyi haƙuri bai kamata ba,bana son na saka ki cikin damuwa ne" Dago fuska tayi tana kallon shi"do you love me? Tambayar ma nata wanna karon dariya ya bashi,sai dai a maimakon yayi dariyar sai ya saki murmushi, "I always do love you,and I will always be loving you for the rest of my life" Haka kawai kuma sai ta tsinta kanta da sakin murmushi,ganin yana kallon ta ne yasa ta saisaita kanta,sannan ta tace "to ni ka tambaye ni" "Me zan tambaye ki? " Ko ni ma ina sonka,and if I can continue living with you? Girgiza kai yayi "A'a ba sai na tambaye ki ba" Zaro ido tayi"saboda me? "Saboda nasan amsar" Nan da nan ta bata fuska tana shirin saka wata rigimar "Jauro but this is not fear,ni fa na fara tambayarka amma ni shine ba zaka tambaye ni ba,is not fear" "To naji tsaya,bari na tambaye ki,do you Love me?ya fada yana kure ta da kallo. Murmushi ta sake tana kyara zamanta,daga tsugunnen da yake ta jawo hannun shi " Zauna kar kafanka yayi tsami " Zama yayi yana tankwashe kafa,tare da ƙara maimaita mata tambayar "do you Love me" Girgiza kai tayi"A'a,i do not love you," Ganin yanda yayi shiru ya zuba mata ido ne yasa tace"I just tell you what is in my mind,but don't worry i can live with you forever,but if you continue to be good,and maybe some day i will love you" Murmushi ya sake saki tunda ta fara magana, "Are we good?ta faɗa "Yes" "Ok to faɗa min dazu tunanin me kake yi" Hannun ta ya saka cikin nashi,ya sumbata "ina tunanin iyaye na ne,dazu in da ace suna raye da muka ji gida,da a dakin ta zaki sauka,babu wanda zata bari ko da harara ya maki,iyaye mutane ne masu muhimmanci wanda da yawa basu sanin haka sai sun rasa su,naso ace na rayu da nawa iyayen,da wallahi sun ga gatan da basu taba tsammani ba,gashi dai yanzun ina da duk wani abinda dan adam ke buƙata a rayuwar shi,sai dai ba ni da wanda zai saka min Albarka,that's very very painful,dan haka ki kyautata ma iyayen ki lokacin da kike da damar haka,ma'ana lokacin da kuke tare,ba sai lokaci ya kure ba,how I wish zan iya ganin su,nayi rayuwa dasu ko da na kwana daya ne, da n..... Rungume shi tayi a jikinta tana shafa bayan shi,"is ok,na san kasan Allah baya barin wani dan jin daɗin wani,in da kuwa yana yi,da bai raba tsakanin uwa da ɗa ba,da bai raba masoya ba,shi Allah mai yin duk yanda yaso ne,a kuma sanda ya so,Kuma ko yanzun lokaci bai kure ba,kama da damar da zaka masu babban kyauta wanda suna can amma kuma suna maka Addu'a,suna mai Alfahari da kai da abinda ka mallaka " Dagowa yayi yana ƙara rike hannun ta"faɗa min,me zan yi,me zan yi da zan saka masu farin ciki" "Ka sani mana,ga ba Sadakatu Jariya ba,sadaka mai gudana,misali gina rijiyoyi in da ake matsalar ruwa,gina masallaci a inda ake da buƙatar haka,misali cikin ƙauyuka za'a bincika,ko kuma kananun unguwanni,ga kuma Islamiya,duk kana ina yi da niyar duk wani abin Alkhairi da aka gudanar Allah ya kai lada gare su" Rungume ta yayi sosai, Jin matsar yayi yawa yasa ta saka ihu tana fadin ya sake ta, Dariya ya fara"na gode sosai Sumy,nasan da haka amma kuma wannan tunanin bai taba zuwarmin ba,na gode Allah ya maki Albarka " "Amin" Ta faɗa tana mikewa,"yau me za'a dafa " "Kaji gulma dama kina tambayata me zaki dafa ne? Turo baki tayi,kafin tayi magana yayi saurin faɗin" Kin ga mai da fushin yau ni zan mana girki da kaima" "La da gaske,dama ka ita girki ne? " Uhmm,yau zaki ci girkin maza," "To me zaka dafa mana" "Chinese food" "A'a ni dai bana so,ba dai wanda suke saka Tana da tsutsa ba" Zaro ido tayi tana rufe baki da tafin hannun ta"ba dai kana cin tsutsaba,and you Kiss me" Dan shiru yayi kamar me tunani "to wani lokacin dai na kan dan ci kaɗan" "Tsutsan,? " Ummm" Da gudu ta buɗe bandakin da ke falon ta shiga kakarin amai, Dariya yake,domin duk daukan shi wasa take,sai dai kan ya Ankara har ta fara sheka amai, Da sauri ya bita bandakin,ya shiga shafa bayanta "wasa fa nake maki,ban taba ci ba,ni fa a England nayi karatu ba a China ba," To abu ne ya zo ba control dan haka sai da tayi Amai sosai, Shi ya taimaka mata ta dawo falo ta zauna tana sauke numfashi, Gabaɗaya duk ya shiga damuwa,dan bai ɗauka abin zai yi serious haka ba, "Kiyi haƙuri sumy duk ni naja maki" "Is ok,amma dai kar ka ƙaramin irin haka bana so" "I promise ba zan ƙara ba" Mikewa tayi "muje na ga yanda zaka yi girkin" Murmushi yayi yana rike hannun ta,"ai kuwa zaki gani"..... *🍂JAURO🍂* (MAI ANGUWA) Story & Writing By JIDDARH UMAR 🌟🌙🌙🌙🌙🌙🌙🌟 *🌙✨MOONLIGHT WRITER'S ASSOCIATION🌙✨* https://m.facebook.com/Moonlight-writers-association-109698351308376/ *'''We are the moonlight writers we shine all over the world.''🌍'* ✍️✍️ بِسم الله الرحمن الرحيم ~~~~~~~💞💞~~~~~~~ *Ban yarda wani ko wata su saka min littafi a shafin su ko su mai da min littafi Audio ba tare da izini na ba* *50* *Wannan littafin nawa mai suna a sama na mai da shi na kuɗi,tare da Yar Tsanar Zinare,wanda yake son guda ɗaya dari uku 300,guda biyu 500 dari biyar, Hauwa Umar,Zenith Bank,2284905309,sai shaidar biyi ta wannan number 08141644865* Kicin suka shiga,jawo mata kujera yayi yace ta zauna, Kallon shi kawai take tana jira taga yanda zai yi,kila ma ko gas bai iya kunnawa ba, Gani tayi ya buɗe kwandon da suke ajiye Albasa ya dauko babba guda ɗaya,sai kayan miya Fresh su koren tattasai da mai kalam green da ruwan ƙwai,sai Attarugu da green beans da carrot,ya hada a karamin kwando ta wanke sosai ya cire dattin da kuma ya'yan ciki, Daga tsayen da yake ya cikin kwarewa ya yayyanka su kanana,ko wanne ya ajiye a gefe,sannan ya daura madaidaicin tukunya a kan gas ya tsiyaya man gyaɗa dai dai wanda zai isa,kafin yayi zafi taga ya buɗe ledan taliya guda daya ya raba biyu ya mai da rabi inda suke ajiyewa,wanda zai yi amfani dashi kuma ya kakkarya gida huɗu,suba kanana ba su ba manya ba, Albasa kaɗan yasa a man sai tafarnuwa karamin ɗaya,suna soyuwa ya kwashe ya zuba a karamin pleat, Mikewa tsaye tayi da sauri tayi in da yake tsaye,ganin amaimakon ya zuba yankakken kayan miya amai ya soya ta shine ya zuba taliya amai yana soyawa, "Jauro me haka kake yi,ba a soya taliya,kayan miyan can zaka zuba" Juyowa yayi ya kalle ta yana ci gaba da juya taliyar,"ke dai kawai ki zauna ki jira,idan har baiyi dadi ba nayi Alkawarin kai ki gidan abinci ki ci duk wanda kike so" "Amma k... " Maida ita yayi ya zaunar inda ta tashi "ki yarda da ni,zauna" Ba yanda ta iya komawa tayi ta zauna tana jiran taga ikon Allah,soya taliya,bari dai taga iya gudun ruwan shi, Tana kallo har saida taliyan ya soyu kamas,sannan ya kwashe a kwani kwando,ya sauke tukunyar ya rage man,sannan ya kawo green beans ya soya na ɗan wani lokaci tare da yanke yanken da yayi,ya kwashe da ban,sannan ya kara zuba ruwa madaidaici ya rube, Firig ya buɗe ya dauko naman Kazan dake dungule a leda ya wanke ya yanka kanana sosai,sannan ya zuba a tukunyar tare da kayan kamshi da magi,minti goma ya buɗe ya zuba wannan soyayyen taliyar ya juya sosai,ya rufe,sai da ya kusa tsotsewa sannan ya kawo kayan miyan daya tsoya ya juye aciki ya kara juyewa, Tuni ta fara hadiye miyau jin yanda wani irin kanshi ke dukan hancinta,sai dai haushin ta daya idan ta duba tukunyar da kuma yawan taliyar sai taga ita kanta ko duka aka juye mata ba lallai bane ta koshi,balle su har rai uku, Tana kallo ya rage wuta sosai, Sannan ya kwashi kayan da yayi amfani dasu ya wanke tas ya kife, Zuwa lokacin girkin ya gama tsotsewa ya sauke, wasu pleat din ya dauko ya raba abincin kashi uku ta zuba ma kowa sannan ya saka a babba tire ya kai falo ya dawo ya dauki lemun kali babba guda daya da cup sai cokali, "Ranki ya daɗe muje ko" Tashi tayi tabi bayan shi,"bari na kira Aisha" "Ok" Ba jimawa sai gashi sun dawo tare, Zama suka yi suka yi Bismillah,diba tayi a cokali takai baki, Kallo ta yake,yana jira yaga Reaction din ta, Lumshe ido tayi ta bude tana lasan lip dinta,murmushi ta saki"duk da ƙanshin mai matukar jan hankali ne,kamar yanda kyanshi ke da daukar hankali saboda yanda ka tsara,ban ɗauka daɗin zai kai haka ba,gaskiya yayi daɗi sosai,na kuma yaba " Bai bata amsa ba sai murmushin dake fita daga fuskar shi, Cikin natsuwa suke cin abincin,kiranshi aka yi a waya,dan haka ɗauka yayi yana dan matsawa gefe daga inda suke, Yana kammalawa ya juyo ya dauki cokali ya saka a pleat,sai dai maimakon da dibo taliya sai gani yati yayi ba komai a pleat din, Kallon ta yayi ya kalli pleat din dake gaban ta,nashi ne kuma saura kaɗan ma ta karasa cinyewa, Yama kasa ce mata komai,sai da ta kammala ta haɗa pleat din sannan ta mika ma Aisha"haɗa ki wanke harda tukunyar,sai ki share kicin din,yanzun zan zo nayi morping" Amsawa tayi ta kwashi kaya tayi kicin, "Me yasa zaki cinye min abinci? Ta gi ya fada. " Ban koshi bane,kuma abincin yayi daɗi " "Shi yasa nayi kaɗan ai" "Wannan ai mugunta ne,kasan zai yi daɗi badan ka yi yanda kowa zai koshi ba,ni ko yanzun na samu ƙari ƙarawa zan yi" "Kuma ba zaki samu ba" Turo baki tayi"amma dai kasan hakkin ka ne ciyar da ni har sai na koshi,amma kai na lura sam baka son haka" "Hakan ba matsala bane in dai har zaki rinka motsa jiki," Da sauri ta girgiza kai"a'a bana so,ba zan je motsa jiki ba,"sai kuma ta marairaice fuska ta matso in da yake"Jauro,dazu kace in bari mu dawo gida sai mu yi magana" "Wanne? " Na batun koyarwar" Ajiyar zuciya ya sauke sannan yace"naji ki bari zan yi magana da wani me makaranta da na gani sakan layin mu,sabon makarantar gomnati ne,idan kin ce zaki je na cikin gari kullum nawa zaki rinka kashewa kudin abin hawa,idan kin yi lissafi a wata babu wani abunda zaki samu,amma idan anan ne kusa da gida ba zaki samu matsalar komai ba" Cikin tsananin murna da farin ciki ta rungume shi"na gode sosai Allah ya biya ka" "Kiyi Addu'a Allah yasa ki samu" "In sha Allah zan samu" Sai zuwa ƙarfe takwas sannan ya sallame ta akan zai kwana a wurin aiki ranar sai kuma tara na safe zai dawo,dan ya kwantar mata da hankali dan yaga ta fara fadin duk girman gidan su biyu kawai zasu kwana,tace karta damu,gobe da da zaran ya dawo zai kai ta gida ita da Aisha,shine fa ya samu suka rabu lafiya da murnar ta akan gobe zata gida. Ganin ta wuce ne yasa ta buɗe firig ta beda masu kindirmon da tayi,tasa suger suka sha, Sai zuwa goma sannan ta kashe komai dama tuntuni ta kulle ko ina,suka shiga suka kwanta, *Asuba ta gari Sumy* Washegari tunda Asuba ta tashi ta gyara gidan,ka kafin ƙarfe tara har ta gama har abin kari sunyi wanka, Shi kawai take jira, Bai shigo gida ba sai kusan goma da rabi,zuwa lokacin gaba ɗaya ji take ranta a bace,haushin komai take ji, Ganin sha ɗaya tayi ne yasa ta zauna ta fara sharan hawaye, Ita kuma Aisha tana buga Game a wayar ta, Shigowa yayi da sallamah,ya nufe in da take zaune a kujeran madubi, Riko hannun ta yayi kawai ya mikar da ita tsaye"Sorry I'm late,muje na kai ku"sai lokacin ya lura da fuskarta, Subhanallah ta fada yana saka fuskarta a tsakanin tafin hannun shi"me ya faru,me ya same ki" Kokarin saka kuka take,yayi saurin katse ta"Shiiiii,ya isa haka,nasan ni ne,amma ba gashi na dawo ba,kin ga mai da hawayen in ba haka ba kika bari fuskarnan nayi ya koma ja,to zamu fasa tafiyar,sai dai nasa a maida ita " Da sauri ta share hawayen daya zubo mata"me ya saka daɗe,bayan kasan ina nan ita jiran ka" Rungume ta yayi "shi yasa nayi sauri na dawo,domin nasan rigimatu na tana jira na,muje nasan Mama na nan na jira" Daukar Hijabinta ta yi ta saka sai hakkin Aisha data mika mata,har sun shiga mota tace ya tsaya tayi mantuwa,komawa tayi ta dauko roban kindirmo ta dawo sannan suka tafi, Ko jira ya gama parking dakyau ba tayi ba ta fita da gudu tana kiran sunan Mama tun kafin ta karasa shiga cikin gidan, A tsakar gidan ta samu Mama tana wanki wance jin muryar mai kiran ta ne tasa ta tsaya tana kallon kofar gidan, Tana shigowa ta taci birki a tsakar gidan tana wurwurga idanun ta don ganin ta ina zata ganta,ta daki ko ta kicin,idanun sune ya fada cikin na juna ai kuwa tsalle biyu tayi sai gata rungume a jikinta,tana dariyar farin cikin, Ita kanta Mama dariyar take, "To sake ni karki karasa ni"ta fada tana dago ta, Suna kara haɗa ido kuma da Mama sai fashewa tayi da kuka ta kara rungume ta, Dariya ta saka" A'a me kuma na kuka bayan gaki a kafaɗa ta" "Mama naji kewar ki" Ta faɗa tana kara sautin kukan ta. Daga bayan su suka ji ance"Mama to ni ba zaki rungume ni ba,ko dai ni baki ji kewata bane" Murmushi ta sake"wane ni nace banji kewar Auta na ba,maza zo nan naji dimin ki"da gudu ta karaso ta rungume duka. Wasu yara ne suka shigo da manyan ledoji suka ajiye suka fita, Daki suka shiga ta faɗa kan gadon Mama tana mulmula "gado nayi kewar ka sosai,do you miss me" "Mama Uncle Jauro na waje " Salati ta saka tana kallon ta"dama tare kuke shine baki faɗa min ba" "Nifa Mama mantawa nayi" "Kin ga Aisha fita ki ce masa ya shigo" "To Mama" Ta fita kuwa da gudu,sai gasu tare, Sun gaisa cikin mutunci sosai ta masa godiya ta saka masa Albarka, Aisha ya faɗa ma ta faɗa mata sai zuwa yamma zai dawo ya dauke ta, Sun jima suna hira sosai na bayan rabuwa da irin kewar Mama da ta ji, Ita ta karasa wankin ta kuma daura girkin rana wanda tayi dambun shinkafa, Mama kuwa duk inda tayi tana bin ta da ido tare da godewa Allah, Misalin karfe hudu na yamma ta idar da sallar kenan ko tashi bata yi ba saman darduma ta fara jin hayaniya tsakar gida da kuma kuka dake tashi, Cikin sauri ta shafa Addu'a ta fito, Tsayawa tayi a ƙofar daki tana kallon su domin tama kasa karasowa, Aunty Amina ce rungume jikin Mama tana rusar kuka, Kafafunta ko takalmi babu,kuskanta ya kumbura sutum dan idonta daya kamar zai rufe saboda kunburi, Ga jikin ta dun satin duka ta ko'ina......... *🍂JAURO🍂* (MAI ANGUWA) Story & Writing By JIDDARH UMAR 🌟🌙🌙🌙🌙🌙🌙🌟 *🌙✨MOONLIGHT WRITER'S ASSOCIATION🌙✨* https://m.facebook.com/Moonlight-writers-association-109698351308376/ *'''We are the moonlight writers we shine all over the world.''🌍'* ✍️✍️ بِسم الله الرحمن الرحيم ~~~~~~~💞💞~~~~~~~ *Ban yarda wani ko wata su saka min littafi a shafin su ko su mai da min littafi Audio ba tare da izini na ba* *51* *Wannan littafin nawa mai suna a sama na mai da shi na kuɗi,tare da Yar Tsanar Zinare,wanda yake son guda ɗaya dari uku 300,guda biyu 500 dari biyar, Hauwa Umar,Zenith Bank,2284905309,sai shaidar biyi ta wannan number 08141644865* Cikin tsananin tashin hankali ta karaso inda suke tsaye,gabaɗaya ita kanta jikinta har rawa yake tsabar tsoron irin ganin halin da ƴar uwarta ke ciki,ga Mama tsaye ta kasa magana,gaskiya wannan abin yayi yawa,duk da yana dukanta amma na wannan karon na daban ne, Zamewa tayi daga jikin Mama ta zauna a kasa tana cigaba da kuka, Dagota tayi daga zaunen da take tana rike hannun ta tasaka ihu tana dafe hannu, Da sauri ta saki mata hannu,tana jin hawaye na zuba daga idonta,bata taba ganin yayar nata cikin irin wannan yanayin ba sai yau, Cikin dubara ta taimaka mata ta tashi suka shiga dakin Mama,wacce suka bari tsaye ta kasa yin komai, Zaunar da ita tayi kan ga,ɗan kwalin kanta ta cire tana kokarin goge mata hawaye,sai dai tana kaishi saman fatan fuskarta ta saka ƙara tana kauda kai,dan ko'ina aka taɓa a jikinta duk ciyo yake mata, Ajiye ɗan kwalin tayi gefe tana share hawayen ta,dole ne ta zame masu ƙarfin guiwa,ƴar uwarta tana bugatar wacce zata kwantar mata da hankali ta fahimci ciyon da take ji, "Aunty Amina" Ta kira sunan ta, Dago kunburarrun idanun ta tayi ta kalle ta, "Aunty Amina me ya faru,ba zan tambaye ki wa ya maki wannan ɗanyen aikin ba,dan nasan ba zai wuce Baban Amir ba,me ya faru? Lumshe ido tayi tana wasu hawayen na ƙara zubo mata,duk da ba karamin raɗaɗi idon ke mata ba,sai dai bai kai raɗaɗin da zuciyarta ke mata ba, " Ada ina ƙoƙarin in ga na jure komai da komai,dan gudun bata ma Baba rai,da kuma tada ma Mama hankali,na ɗauka zan iya jurewa nayi haƙuri har nayi maganin matsalar da Addu'a, Sai dai na kasa,na kasa Sumaiya,Dahir kashe ni kawai yake da buƙatar yi,nasan ni ba komai bace a wurin shi face abinda ya saka makudan kuɗi ya siya,a yanda yake gani,saboda irin kuɗin shi da Baba ta amsa,bai dauke ni da daraja ba,ni ban isa in hana shi duk abinda yayi ni ya ba, Ban taba faɗa ma kowa irin niman matan da Dahir ke yi ba,amma yan uwan shi duk sun sani amma daura laifin haka suke a kai na har da uwar shi, Har mata yake daukowa ya yawo min gida,ban isa in yi magana ba,basu taba faɗa mashi abinda yake ba kyau ba,amma sun daura laifi a kaina, Yau kusan kwana shida kenan da Mamar shi yan uwan shi suka zuga ta wai ta dawo gidan mu da zama saboda Dahir duk abinda ya samu ni kadai da yaya na yake kashe ma,ba karamin daɗi nake ci ba kuma sai yanda nayi dashi,to yanzun ta dawo gidan mu da zama, Shine yasa aka kyara mata ɗayan dakin shi,inda anan yake ajiye yan matan na shi, Yau da misalin karfe goma sha ɗaya na safe na gama aikina na kwanta sai gashi ya shigo dakin wai in fito yayi bakuwa, Kallon shi nayi na kalli yarinyar da ke da shirin banza a jikinta nace su zauna anan falo in da nake zaune suyi hiransu amma ba zan fita ba, Zan hannun yarinyar yayi wai suzo su shiga Uwar daki na,su barni a falo, Ba zan iya ba,ba zan iya jurewa ba,dakina na sunna,gadona na sunna,dan haka ba tare bakin kofa nace ni kuma basu isa su shigar min dakin ba,shine,shine"fashewa tayi da kuka ta faɗa jikin Sumayya "shine ya haɗa kaina da kofa ya buga,duka na ya fara yi dan kawai na hana shi aikata ɓarna a saman gadon sunnan mu,ya fini ƙarfi nisa ba kusa ba,ganin idan na zauna zai iya min rauni ne yasa da gudu na fita ina ihu na shige dakin Mamar shi,Sumaiya you can't believe if I tell you abinda ya faru a dakin Mama," "Na yarda da ke Aunty Amina,nasan ba zaki taɓa min karya ba,me ya faru dakin Mama" Cikin shesshekar kuka tace"ina shiga na ɓoye a bayanta ina kuka ina faɗa mata abinda ke faruwa,sai gashi ya shigo,wai karya nake mashi,zagin iyayen shi nake rayi,sannan dan ya kawo abokiyar kasuwancin shi tazo mu gaisa shi ne yake ta zagin yarinyar na hana ta shiga daki na, Shine Mama ta jawo ni daga bayanta ta shiga koda min Mari ita shi kuma suka shiga duka na,da kyar na iya kwace kaina na shige daki na na kulle ƙofa,har yana faɗa ma Mama dake kiran sai dai in ba zan fito ba,wai ta dai na wahalar da kanta in dai ni ce da kaina zan fito,in kuma naga dama na wuce gidan uba na kwadayayye yasan kona je gida dole zai dawo da ni,wallahi Sumaiya wannan karon Aure na da Dahir ya kare,ko da Baba zai kashe ni ba zan koma ba,bazan koma in da ba'asan daraja ta ba,ba a san mutunci na ba,na gaji ba zan iya ba kuma kashe ni suke son yi"ta faɗa tana ƙara rushewa da wani kukan mai taba zuciyar mai saurare balle uwa, Rungume ta tayi"ba in da zaki koma,Allah ma ya gani kin masa biyayya fiye da inda zaki iya,dan haka wannan abun ya isa haka ke ma ya ce kamar kowa" Dagowa tayi daga jikin Sumaiya tana kallon Mama dake tsaye bakin kofa tana jin su"wallahi Mama idan har Baba yace sai na koma guduwa zan yi sai dai na shiga duni..... Da sauri Sumaiya ta rufe mata baki "ba zaki taba barin gida ba Alhalin shi shedanin daya aikata bai bar gida ba,ba zaki shiga duniya ba" Ji sukayi Mama tace" Tabbas ko ni ba zan bari ki koma ba,koda kuwa zamu bar wannan gidan a tare" Daga tsakar gida suka ji ance "ai kuwa sai dai ku bar gidan a tare,domin ba zata mai da ni mutumin banza ba,ta zubar min da kima, Ina wurin aiki mijinta ya kira ni yake sanar da ni dibar Albarka da ta masu shida uwar shi,har da zagin rashin mutumci,dan haka kafin raina yakaiga baci maza zoki barmin gida ki koma gidan mijinki ki bashi haƙuri shida uwar shi" "Wallahi ba zan koma ba,koda zaka kashe ni babu in da zan koma" Cikin jin haushi ya doso in da take"ai kuwa ba dai a gina ba,dole ki koma kona miki dukan kawo wuƙa " Tare bakin ƙofar Mama tayi"bancin irin wannan dukan da aka mata na jeki ki mutu,shine zaka ce zaka mata dukan kawo wuƙa,sai dai in kashe ta kake son yi,ni kuma ba zan yarda ba wannan karon dan ina ji ina kagi ba zan bari ka halaka min yata ba,tunda na lura ba kasan muhimmancin ta ba" Na zato ba sammani sai jin saukar mari suka yi wanda ba fuskar kowa ya sauka ba face na Mama, Duk zabura suka yi cikin tsananin mamaki da tsoro abinda basu taɓa gani ba, "Ni zaki faɗa ma bansan darajar ta ba,darajar mace ya wuce gidan mijinta,dole sai ta koma ko kuma ta barmin gida" "Ba dai tabar maka gida ba sai dai mubar maka gidan gaba daya" Hannu ya daga zai kai mata wani marin suka ji karan tarwatsewar wani bokitin roba saboda bugun da ta kai masa da iccen dake hannun ta, Ma tsowa tayi in da yake tsaye ta tsaya cikin bushewar ido da zuciya irin wanda takai makura wurin ɓaci,ta na kallon shi ido cikin ido"Saboda baka dauke dauke ta amatsayin matar ka mai kima wacce kuka sha wahalar gina rayuwarku tare ba,saboda ka maida ita da ya'yanta ba komai ba,saboda bata haifarma ɗa namiji ba,shi yasa kake mata haka,shi yasa kake kokarin salwantar mana da rayuwar mu,saboda muna ya'ya mata,kana ganin babu wanda zai iya tare mata,ni ban damu ba dan ka tsine min k zageni,sai dai ba zan bari ka kuma cutar min da uwa da yar uwa ba,wallahi tunda baka ji kunyar daga hannu a gaban mu ka Mari mahaifiyar mu ba to nima ba zan ji kunyar in buga maka wannan sandar ba,idan kuma kana ganin ba zan iya ba gaba ta nan ka kuma taɓa ta"ta faɗa cikin tsananin zafin rai,dan wannan samun wurin na Baba ya yi yawa. Tabbas abinda ya hango a idon ta ya tabbatar zata iya aikata wa,haka kawai kuma sai ya tsince kansa da shakkun yarinyar, Sauke hannu yayi cikin borin kunya yace"tunda haka kuka zaba ku tattara ku bar min gida na,bana bukatar ku,har abada bana son sake ganin ku,na baku daga nan zuwa ƙarfe biyar"yana gama faɗar haka ya fita yabar gidan, Zamewa tayi nan bakin kofa tana lumshe ido,ta kasa yin hawaye,bata son tayi kuka ta ƙara ƙarya ya'yanta guiwa,bata son ta nuna masu gazawar ta, Yarda sandan gefe tayi da sauri ta karaso inda take ta tsungunna a gabanta,ita ma Amina da dingishi ta karaso in da suke,rungume Mama suka yi gaba dayan su,yayin da Aunty Amina ta fashe da kuka"Mama ki gafarceni na ja maki,gashi ta sanadiyata Baba ta kore mu yace bai buƙatar ganin mu,ni na haƙura zan koma,zan je na faɗa ma Baba yayi haƙuri zan koma amma ya bar Mama tare dashi,ni na haƙura da rayuwar,kula a can Ajali na yake " Dago su tayi daga jikin ta "babu inda zaki koma,ba zan yarda ina ji ina gani rayuwar ki ta salwanta ba,Bani da farin ciki daya wuce naku,na ganku cikin farin ciki da kwanciyar hankali shine buri na,ina ga lokaci yayi daya kamata ni ma nayi tawa rayuwar cikin yanci tare da ya'ya na," Sallamar wani yaro ne ya katse su,karasowa yayi in da suke ya mika mata wata takarda "Maman Sumaiya gashi in ji Baban Aisha wai na baki" Karɓar takardar tayi gabanta na faduwa,amma bata nuna komai ba sai amsa da tayi ta rike a hannun ta, Juyawa yaron yayi ya wuce, "Mama yanzun ina zamu tafi,? Cewar Amina, Murmushin dole ta kakaro domin ta san inda zasu je can din Asalin matsalar take,sai dai ya ta iya,ba tada in da yafi nan," Gida,gidan mu dole can zamu koma " Jikinsu ne ya kuma yin sanyi,koda yini suka je yi a gidan da yaya suke yi su dawo saboda tsangwama,iyayen Mama duk sun rasu hannun kanin babanta ta tashi gida mai cike da yara,kowa kanshi da nashi kawai yake so,ko abinci in sunje sai ace ya kare alhalin suna kallo,gaskiya da sauran matsala a kasa kenan,amma ba yanda zasu yi,ƙaddara ce da Allah ya riga ya kawo masu,kuma dole su amsheta hannu bibbiyu, Mike wa tsaye tayi"ina ga yanzun ya kamata naje na faɗa ma Baba abinda ke faruwa,ku kuji rani a gida zan je na dawo in ya so in ya bamu daki sai akwashi kayan akai can sai mu kyara,kafin mijinki ya dawo "ta karasa faɗa tana kallon Sumaiya. Addu'ar a dawo lafiya su kai mata,suna masu fatan dacewa da sa'a. Gabaki daya duk zama sukayi suja zuba tagumi kowa da irin abinda ke ci masa rai, Yayin data bangaren Mama Allah kadai yasan halin zullumin da zuciyar ke ciki,dan ta san halin Baban ta,da kuma matanshi,sai dai wannan karon kome za'ayi sai dai ayi amma ba zata kara bari a cutar mata da ya'ya ba,sai dai shima in koran nata zai yi....... *🍂JAURO🍂* (MAI ANGUWA) Story & Writing By JIDDARH UMAR 🌟🌙🌙🌙🌙🌙🌙🌟 *🌙✨MOONLIGHT WRITER'S ASSOCIATION🌙✨* https://m.facebook.com/Moonlight-writers-association-109698351308376/ *'''We are the moonlight writers we shine all over the world.''🌍'* ✍️✍️ بِسم الله الرحمن الرحيم ~~~~~~~💞💞~~~~~~~ *Ban yarda wani ko wata su saka min littafi a shafin su ko su mai da min littafi Audio ba tare da izini na ba* *52* *Wannan littafin nawa mai suna a sama na mai da shi na kuɗi,tare da Yar Tsanar Zinare,wanda yake son guda ɗaya dari uku 300,guda biyu 500 dari biyar, Hauwa Umar,Zenith Bank,2284905309,sai shaidar biyi ta wannan number 08141644865* Tana shiga gidan da sallamah ta gaida matan gidan,Uwar gidan shi da suke kira da Goggo ta tambaya"ko Baba na nan? "Ki shiga yana ciki" Godiya ta mata sannan ta shiga dakin bayan ya bata damar shiga. Ko zama bata yi ba yace"kinji daɗi kin kashe ma yar ki aure sai ki yi yanda kika so dasu,tunda kin nuna ba wanda ya isa dake " Wato har yazo ya riga ta faɗa kenan, Tsugunnawa tayi guiwa biyu a gaban shi,"Baba ka bani dama na maka bayani akan komai" "Babu wani bayani da zaki min,domin na riga nasan komai,ba dai zaman gidan kike son ba,ai gaki gashi sai kiyi,akwai dakin dake kusa da dakin yara babu komai a ciki sai ki kyara ki zauna,ni ba nida karfin da zan ciyar dake da iyalan ki,sannan zan ƙara tuna maki ba kida gado a nan gidan domin babanki ya riga iyayen mu rasuwa,zaman ki anan na ɗan wani lokaci ne sai kiyi ƙoƙarin shawo kan mijinki ki koma," Kokarin danne zuciyarta kawai take yi,tana haɗiye abinda ke taso mata,"na gode Baba,"ta mike tana fita,tsaki yaja yana kyara kwanciyar shi, Tana fitowa ta sami Goggo in da take kyara wuta"Goggo wai in ji Baba ki nuna min dakin kusa dana yara " Da hannu ta nuna mata"gashi can" Dakin ta nufa tana kallo,karamin daki ne wanda ko rabin kayansu ba zai dauke ba,gashi babu windo babu ƙofa,innalillahiwa'inna'ilaihi rajiun,abinda take ta maimaitawa kenan, Sallamah taimata ta wuce, A wani lungun dake unguwar su wanda ba'a cika bi ba,ta tsugunna ta shiga rusa kuka, dan ji take kamar zuciyar ta zai fashe dan irin raɗaɗin da yake mata,kuka take sosai wanda sai da tayi kusan minti talatin kafin ta iya sai_sai ta kanta,bawai danta gaji da kukan ba, Tashi tayi ta goge fuskarta sannan ta kama hanyar gida,zuwa lokacin biyar saura,ta san kudin dake hannun ta kwata_kwata bai wuce dubu uku ba,sai kayan miyar da bai wuce na dari uku ba,dama shi take siyarwa,kuma a yau tayi niyar zuwa kasuwa ta siyo,sai ga zuwan Sumaiya, Tana shiga a lulluɓe ta same Amina tana rawar sanyi,Sumaiya kuma sai sannu take mata, Bata jira komai ba tace ta tashi suje chemis,sai dai ita Amina taki yarda wai sai dai kawai a siyo mata magani ta sha na ciyon jiki, Da yake basu da nisa da kemis shine Sumaiya ta amsa dubu daya taje ta hado magunguna, Tana kallon idon Mama tasan cewa tayi kuka,bancin damuwar dake kwance a fuskarta,sai dai sam ba zata iya tambayar ta ba,dan bata son ta kuma tada mata da wani mikin, Ganin Aunty Amina tasha maganin ne yasa suka fara haɗa kayan cikin manyan buhu ita da Mama, Sai da suka kammala sannan ta fita ta kira mai Adaidaita suka zuba kayan a ciki, Ita take binshi suna kai kayan tare,sai da sukayi mayawa biyu da kaya,ana uku kuma ta dauko Mama da Aunty Amina, Ita kanta hankalin ta a tashe yake ganin irin dakin da su Mama zasu zauna,amma ba tada yanda zata yi, Tabarma suka shimfida ma Aunty Amina ta gefen dakin sannan suka shiga ita da Mama suka share dakin suka kyara,sannan suka shimfida kafet, Katifar Mama dayafi girma suka shinfida,sannan sauran kayan kuma suka hada wuri ɗaya suka loda shi, Gabaɗaya dakin a cike yake ɗan wurin sallah kawai suka bari, Lokacin ma har Ana shirin kiran sallah Magrib, Aisha ce ta shigo dakin tana fadin"Mama zanci tuwo"wanda ba komai ya sa ta fadin haka ba face ganin yaran gidan dake cin tuwo,kuma babu wanda yace mata ta zo ta amsa, Laluba Ajjihunta tayi kwata_kwata abinda ya rage mata bai wuce dari bakwai ba,sai garin masara da take dashi da bai wuce rabin mudu ba, "Nasan yanzun mijinki zaizo yaa kamata ki kira ki faɗa masa inda kike karyaje can bai same ki ba,ni bari naje ya siyo kayan miya na dawo" "To Mama ki kawo na siyo " "A'a bari dai naje" Gyaɗa kai ta yi,sannan da ɗauki wayar ta tana kiran number shi,ganin Aisha na kokarin fita ne yasa tace"ke Auta dauko ga leda can da Jauro ya kawo muga me aciki" Da gudu ta dauko ledojin, Buɗewa tayi,Manyan Gwangwanayen kayan shayi ne da suger Kwali,sai biredi manya sinki biyu,da kuma Chocolate,dasu cake,sai wata Envelop data gani tana buɗewa taga kudi wanda ta kirga taga dubu goma ne cip, Ba ta san sanda ta saki murmushi ba wani irin daɗi na kama ta,karo na farko daya mata abinda ya birgeta kuma ta ji daɗin shi har a zuciyar ta. "Aisha dauko roban kindirmon da muka kawo na zuba maki ki sha kafin a gama abinci" Jin ya dauki kiran ne yana sallamah yasa ta amsa mashi,"idan zaka zo kazo Limawa family house din su Mama ka sauke ni" "Me kuma ya kaiki Limawa? " Is a long Story sai ka zo" "Ok"ya faɗa yana katse wayar. Tashi tayi ta hada wuta a Abaca tunda sunzo da gawayi,yana kamawa ta ɗaura ruwa a kofi,yana yin zafi ta juye a kofi ta Daura tukunya ta kuma saka wani ruwan, Tea mai kauri ta hada a kofi ta ajiye a gefe,sannan ta taimaka ma Aunty Amina wacce Mama ta saka ta zauna tunda Magrib ya gabato ta sha Tea din,sai da ta tabbatar tashanye sannan ta kyaleta, Sai da tayi sallah sannan ta juye ruwan zafin ta taimaka mata tayi wanka ta gasa jiki, Mama ce tace"ina aka samu kayan shayi haka"ta faɗa tana shan kindirmon data diba a kofi, "Kayan da Jauro ya kawo ne,gashi ma harda kuɗi a ciki" Ta faɗa tana mika mata, Amsa tayi tana saka mashi Albarka,da Allah ya gani wannan kudin da kayan ba karamin taimakonta zaiyi ba, "Mama wallahi hankali na ba'a kwance yake ba,kalli wannan dakin fa babu wundo babu ƙofa," "Ai ga labule nan mun saka,kuma wata rana sai labari" Ajiyar zuciya ta sauke tana daukar wayar ta dake ƙara, "Ina ƙofar gida" Abinda ya faɗa kenan, Ji take tamkar tace masa ya wuce kawai ba zata ba, "Gani nan fitowa" Kallon Mama tayi tana marairaice fuska"Mama yazo" Murmushi tayi tana gode ma Allah a zuciyar ta,ko ba komai ta samu sauki ta wurin Sumaiya tunda tana zaune lafiya da mijinta,"tashi ki tafi Allah ya maku Albarka,ki ƙara mai godiya" "Amin Mama" Lekawa tayi in da Aunty Amina take,sai dai tayi barci ko,gashi sai zufa take haɗawa dan har anyi sallah Isha, "Idan Aunty Amina ta tashi ki gaida ita,in sha Allah ina nan zuwa in kara dubata" "Zata ji" Aisha tarakata har kofar gida tashiga mota sannan ta koma gida, Kallon ta yayi yana tada mota"yana ga fuskarki tamkar kinyi kuka" "Ni ban yi kuka ba" "Allah yasa,amma idanun ki sun nuna" Bata bashi amsa ba,dan bata son magana, Tsayawa taga yayi ya siya masu gasasshen kaza, Suna zuwa gida wanka tayi ta saka wani rigar bacci fari tas,iya cinya ko bran bata saka ba tayi kwanciyarta,tana tunanin halin da su Mama ke ciki, Kallon dakin da take kwance tayi,ga AC na tashi,haka kawai ta tsintan kanta da fashewa da kuka,ta ja bargo ta rufe kanta tana cigaba da kuka, Bata ji shigowar shi ba sai jin tayi mutum ya zauna kusa da ita,yaye bargon yayi ya dagota jikin shi gabaɗaya ya zaunar da ita saman cinyarshi,"me ya samu Baby na? Kwantar da kanta tayi saman wuyan shi tana ci gaba da kukan ta,ba komai ne yasa ta saki jiki dashi ba sai sanin da tayi babu abinda zai mata,tunda a tunanin ta bai da wani katabus ta wannan fannin,, "Ni dama Dazu na faɗa amma kin ce ba haka bane,faɗa min me ke damun gimbiyata" Girgiza kai tayi"um,um,is a family matter" Dagota yayi suna fuskantar juna"ni bana cikin family ku Sumaiya,kin cire ni a cikin family ku ko, A tunani na tunda na same ki zaki Bani dangin ki su zama nawa,iyayen ki su zama nawa,amma kin nuna min ba haka ba" Komawa tayi ta kuma rungume shi ta na fashewa da kuka sosai wanda yafi nada ƙarfi,dan sai yanzun ne abun ke ƙara mata ciyo, Jin yanda ta kankameshi tana kuka sosai ne yasa bai dagota ba sai dai hankalin shi ya tashi sosai jin irin yanda take kukan to gara dai ya bar ta tayi ko zata samu natsuwa, Tayi kuka sosai dan sai dai tayi shiru dan kanta yana aikin shafa bayan ta, Dago fuskarta yayi ya share mata hawayen ta da tafin hannun shi,"fada min me ya faru? A hankali ta shiga sanar dashi abinda yake faruwa tun daga farko har komawar su gidan Baba"hankali na bai kwanta da wannan gidan ba,ga kofar dakin Mama abude babu wundo,ina tausayawa rayuwar da zasu yi,in da ace Iyayen Mama na nan da hakan ba zai faru da ita ba,in da ace mu maza ne da Baba ba zai wulakanta taba,inda ace ma... Maida ita yayi ya rungume "shiiii ya isa haka,komai zai wuce,ba gani ba,ai nima ɗanta ne,ki kwantar da hankalin ki,yanzun tashi kuje mu ci abinci" Girgiza kai tayi"a'a na koshi " Bai bata amsa ba sai ɗaukarta yayi a kafada ya wuce da ita dakin shi, Duk irin kauda kan da take tayi sai da yasa ta ci sosai badan ta so ba,sannan suka yi brush, Tana kokarin fita ne ya riƙo hannun ta"yau anan zaki kwana" Girgiza kai tayi "Jauro yau bana jin fitina kabarni naje na kwanta" Jawo ta gaban shi yayi ya rike hannun ta suna nufar kan gado"shi yasa nace ki kwanta a nan saboda nasan baki jin yin magana,kar kiyi min musu pls" Bata jin yin magana dan haka kan gadon kawai ta hau taja bargo ta rufe tana addu'ar barci. Murmushi yayi yana tuna maganar karshe da suka yi da Baffa Haruna kafin su tafi........... *🍂JAURO🍂* (MAI ANGUWA) Story & Writing By JIDDARH UMAR 🌟🌙🌙🌙🌙🌙🌙🌟 *🌙✨MOONLIGHT WRITER'S ASSOCIATION🌙✨* https://m.facebook.com/Moonlight-writers-association-109698351308376/ *'''We are the moonlight writers we shine all over the world.''🌍'* ✍️✍️ بِسم الله الرحمن الرحيم ~~~~~~~💞💞~~~~~~~ *Ban yarda wani ko wata su saka min littafi a shafin su ko su mai da min littafi Audio ba tare da izini na ba* *53* *Wannan littafin nawa mai suna a sama na mai da shi na kuɗi,tare da Yar Tsanar Zinare,wanda yake son guda ɗaya dari uku 300,guda biyu 500 dari biyar, Hauwa Umar,Zenith Bank,2284905309,sai shaidar biyi ta wannan number 08141644865* Alwallah ya dauro, yayi nafila raka'a biyu ɗan godewa Allah,ya jima yana Addu'a sosai kafin ya shafa ya nannaɗe Darduma ya ajiye inda ake ajiyewa,sannan ya hau kan gadon ya ja bargo ya shige, Kallon ta yake yanda take barci cikin kwanciyar hankali tamkar wacce ba tada wani matsala, Murmushi yayi a hankali yakai hannun shi ya gyara mata sumanta daya sauko ya rufe mata fuska, Gabaɗaya idan yana kallon ta ji yake yana shagala,bakin shi ya kai dai-dai nata ya bata light kiss, Ji yayi ta sake ajiyar zuciya sannan ta juya mai baya, Matsowa yayi ya rungume ta,yana turo hannun shi ta cikin rigarta yana sauke ajiyar zuciya,ganin hakan bazai mai bane yasa ya zame mata rigar gaba ɗaya yayi wulli dashi, Cikin barci taji gabaɗaya tana shiga cikin wani yanayi tun daga sama har kasa,wani iri take ji,kamar dai irin wanda take jin daɗin abinda ake mata,wanda hakan ne ya tilasta mata buɗe ido, Ji tayi kamar an manne a jikin ta,sannan ga hannun mutum yana yawo a jikin ra da babu rigar da ta san ta saka, tsoro ya kamata,cikin rawar murya ta kira sunan shi dan ta tabbatar ko shi ɗin ne"Jauro" "Umm" Ya amsa mata, "Kaine" "Umm" "I'm scare what ar you doing? Ta faɗa tana juyowa gabaɗaya tana fuskantar shi tare jawo bargo da sauri ta na ƙoƙarin rufe jikin ta, Riƙe bargon yayi" Please karki rufe mun abinda yake halal na,nasan is will not be easy for you saboda baki sona ki bani dama ta,amma ina rokon ki Albarkacin halalta mana ta hanyar aure da Allah yayi,da kuma Alƙawarin da yama macen da duk ta faranta ma mijinta rai,karki hana ni,wannan shine aure,kuma shine rayuwar aure,ki bani damar da zan rayu dake har a bada akan sunnah " Ya faɗa yana yin rau_rau da ido cikin niman amincewa, Jikinta yayi sanyi,domin kamar yanda ya faɗa Alkawarin da Allah ya ma maccen data farantawa mijinta haka kuma ta san wanda Allah yama duk wacce bata amincewa mijin ta ba"but I'm not ready" Haɗe goshinsu yayi wuri ɗaya "ki bani dama I will make you ready now,ba zaki ji zafi ba I promise" Shiru kawai tayi tana kallon shi,tama rasa ne zata yi,ita Allah ya gani sam bata shirya ma wannan lamarin ba, kuma a yanda take ganinsa gabaɗaya shi a shirye yake"na amince,amma ɗan Allah Jauro kayi a hankali ni dai duk da bansan iya karfinka ba,duk da kwanaki na nimeka amma baka bani dama ba, i wonder what change your mind,and m...... Haɗe bakinsu yayi wuri ɗaya ba tare daya bata damar yin magana ba, Cikin ƙanƙanin lokaci ya saka ta tahau layi,domin kuwa youghot din da suka sha dazu shi ya haɗa masu,Ayaba,da madaran ruwa na gwangwani,sai kanun fari da zuma,shi ya haɗa ya niƙa masu,ya san aikin da zai masu a jiki idan ka dauki amfanin ko wani daya acikin su,to balle an haɗa, Kafin zuwa wani lokaci har ta fita hanyacinta,dan gabaɗaya ta gama jikewa,saboda irin romancing din ta da yake yi, Ya dauki kusan mituna arba'in yana tsuma su ta yanda saida dukkannin su suka jigata suka matsu da juna kafin ya fara gudanar da harka, Saboda yanayin da suke ciki na muradin juna hakan ne tasa bata wani ji zafi ba,saima bada haɗin kai da tayi suka mori junan su, Sai da komai ya lafa sannan ya dauke ta ya kaita banɗaki, Tare suka yi wanka,duk irin nunnokewar da take yi,dago kanta yayi suna fuskantar juna"me yasa kike kauda kanki?ba na son haka,domin daga yau ba kiɗa abin kallo daya wuce jiki na,kamar yanda nima haka,zan kalle ki a duk lokacin dana ga dama,zan nime ki aduk lokacin dana ji ina son haka,kema kuma ina son a duk lokacin da kika ji kina buƙata na ki nime ni,jiki na naki ne,kamar yanda zuciyata take naki,dan haka karki kara dukar da kai a duk lokacin da muke tare"ya faɗa yana zame towel din dake daure a jikin ta ya ajiye gefe, Kokarin lumshe ido take,da sauri ya busa mata iskar bakin shi,wanda haka yasa dole ta buɗe idon, Sumbatar goshinta yayi sannan yaja hannun ta suka shiga cikin bahon wanka wanda ya cika da ruwan zafi,ya zaunar da ita,sannan shima ya zauna, Lumshe ido take tana ɗan cije leben ta,jin yanda dumin ruwan zafin ke ratsa ta, "Wash_wash" Yake faɗa yana dan yarfe hannu, Kallon shi tayi yanda yayi wani day_daya cikin ruwan zafin,wanda ko ita bata baje haka ba"me kake yi? Ta tambaye shi cikin mamaki, "Ina taya ki gasa jiki ne," "Kamar ya? " Muma maza muna da bukatar gasa namu jikin idan anyi Dis_virgin din mu,nima saurayi ne ke kika fara farke ni a leda,kamar yanda na buɗe ki,kinga dukkan mu muna bukatar ruwan zafi" Ita dai tunda take bata taba jin inda aka gasa namiji ba dan yayi dis Virgin kanshi,sai akan Jauro, Mikewa yayi"bari na canja maki ruwa idan kin gama sai ki yi wankan tsarki,bari naje na gyara wurin kwanciya " Gyada mashi kai kawai tayi, Canja mata ruwa yayi sannan yayi wankan tsarki ya fita. Ajiyar zuciya ta sauke tana lumshe ido jin daɗin yanda ruwan ke ratsa ta. Koda ta fito har ya kammala kyara masu wurin kwanciya,lokacin ƙarfe sha biyu tayi, Ji taji ya dauke ta cak,ya zaunar abakin gado,ya tsugunna a gabanta yana ƙoƙarin tattare towel din dake jikin ta, Da sauri ta hade ƙafa "me zaka yi? Ta tambaya a tsorace, Dago kai yayi ya kalle ta,gani yayi duk sai wani zaro ido take yi" Zan duba ne" "Me zaka duba" Tana ƙara matse kafa, "Ko nayi ɓarna," Ganin yanda duk ta fara tsoracewa ne yasa yace"kinga dubawa kawai zan yi in banji maki ciyo ba,ba wani abu bane ki kwantar da hankalin ki,karki manta mijinki likita ne,so Trust me ok" Jinjina kai tayi sannan ta fara buɗe kafar a hankali, Da tocilan wayar shi yayi amfani ya haska, Babu laifi bata ji ciyo ba,sai dai ja da wurin yayi saboda baƙon daya kawo mai ziyara, Yatsa yasa ya shafa kofar wurin kamar zai tura, Zabura tayi tana dake kafadarsa, Murmushi yayi ya mai da mata towel dinta,mikewa yayi tsaye"babu komai a wurin,you ar fine " Buɗe dirowa yayi da dauko mata wani rigan bacci mai dan kauri ya saka mata sannan yaja masu bargo ya rungume ta,sumbatar goshinta yayi"good Night Baby " Lumshe ido tayi,tun tana jin motsin shi har taji shiru alamun yayi barci, Bude idanun ta tayi tana kallon fuskar shi,ajiyar zuciya ta sauke,lallai wani haɗin sai Ubangiji,in ba haka ba kamar yanda take da kyau wa zai kalli Jauro ya ce ita matar shi ce,in ba yanzu da take kokarin saka shi ya canja ba da dubara,sai dai in ya dauki wanka yanda kasan matashin yaro dan sha takwas haka yake komawa,a yanda yake ɗin nan wa zai ɗauka ya mallaki makudan kuɗaɗe,kadarori,da kuma,dabbobi,a shekarun shi,ita kanta bata fahimci wani irin mutum bane shi sai yanzun da suke rayuwa tare,ƙoƙari yake kawai ya samu farin ciki ta bangaren ta, Murmushi tayi,tuna wai yana gasa kanshi shima,hannu takai ta shafa fuskarshi a hankali,yau ya jiyar da ita daɗin da batasan dashi ba,irin wanda bata taba sammani ana samu ta wannan fannin ba,ƙila ma dazu tayi kukan daɗi dan wallahi gabaɗaya yasa ta fita haiyacinta,,ko ba komai ta gode ma Allah daya bata shi a masayin miji,domin bata taba tsammanin yanada wayewa da sauƙin kai ba irin haka, Haka taci gaba da tunani har barci ya dauki. Washegari da safe tare suka yi sallah Asuba sannan suka koma suka kwanta, Ƙarfe takwas da rabi ya tashi,share gidan yayi, sannan yayi morping, Arish da kwai ya soya sannan ya dafa ruwan shayi ya zuba a fulas,abincin kuma ya zuba a kula,ya ajiye mata a inda suke cin abinci,ya koma yayi wanke-wanke, Ganin ƙarfe goma saura ne yasa ya koma daki yayi wanka har ya shirya tana barci, Lekawa yayi saman gadon ya taba jikin ta dan ya tabbatar lafiyar ta kalau,kuma babu zafi komai daidai, Takarda ya yanka ƙarami ya rubuta mata dan short note sannan ya ajiye kusa da wayar ta ya fita. Koda ta tashi kusan ƙarfe sha ɗaya na safe, Dubawa tayi gefen ta sai dai baya nan,tashi tay ta buba banɗaki baya ciki,dan haka haɗa ruwan ɗumi tayi sannan tayi wanka,tana fitowa ta shirya cikin daya daga cikin Atamfar data gani acikin kayanta dinkin doguwar riga ya fito ya mata kyau,sai wani ƙyalli Amarci da take yi, Ganin har ta kammala shiryawa bai shigo ba yasa ta dauki wayar ta danta koma falo ƙila yana can, Tana jawo wayar wani karamin takarda ya faɗo,ɗauka tayi ta buɗe, Komawa tayi kan gado ta zauna bayan ta karanta abinda ke cikin takardar..... *🍂JAURO🍂* (MAI ANGUWA) Story & Writing By JIDDARH UMAR 🌟🌙🌙🌙🌙🌙🌙🌟 *🌙✨MOONLIGHT WRITER'S ASSOCIATION🌙✨* https://m.facebook.com/Moonlight-writers-association-109698351308376/ *'''We are the moonlight writers we shine all over the world.''🌍'* ✍️✍️ بِسم الله الرحمن الرحيم ~~~~~~~💞💞~~~~~~~ *Ban yarda wani ko wata su saka min littafi a shafin su ko su mai da min littafi Audio ba tare da izini na ba* *54* *Wannan littafin nawa mai suna a sama na mai da shi na kuɗi,tare da Yar Tsanar Zinare,wanda yake son guda ɗaya dari uku 300,guda biyu 500 dari biyar, Hauwa Umar,Zenith Bank,2284905309,sai shaidar biyi ta wannan number 08141644865* Kara kallon takardar tayi tana turo baki,tare da maida takardar ta ajiye, Ko wata Amarya a washegarin daren ta na farko tana farkawa zata ganta rungume a jikin mijinta suna shan dumin juna,wata kuma yana gefen ta yana kallon ta yana jira ta tashi,ya tarbeta dalallausar murmushi,amma ita sai wasika daya ajiye mata akan:Good Morning Hayati,idan kin tashi kiyi wanka da ruwan dumi,akwai abinci a falo ki ci,ina da uziri amma bai kaiki muhimmanci ba,i Love you; "To idan be kai ni muhimmanci ba why going out" Ta fada tana wucewa falo dan ta karya, A ta ɓangaren shi kuwa sai bayan sallah Azahar ya kammala abinda zai yi,sannan ya shiga mota,bai tsaya ko'ina ba sai Limawa a ƙofar gidan Baba, Ya jima a ƙofar gidan bai samu wanda zai aika ba,kamar ance mai ya kalli gefen shi sai gashi ya hango Auta tana tahowa Alamun daga aika take, Ajiyar zuciya ya sauke,sannan ya sauka daga saman mashin din da yake,dan da mashin yazo, Sunanta ya kira yana daga mata hannu "Auta,Aisha" Jin ana kiranta ne yasa ta juyo,ai kuwa tana hangoshi ta hau washe baki da gudu ta karaso inda yake ta rungume shi tana dariya, Shima dariyan yake"ina kika fito haka? "Mama ce ta aike ni" "To ƴar mama,ya jikin Aunty Amina? " Ta ji sauki " "Sosai? Ya tambaya yana son tabbatar wa. Jinjina ki tayi" Sosai" "Tana tafiya" "Eh tana tafiya sai dai tana dingishi" "To jiki ciki ki ce mata inji ni wai dan Allah tazo ina son magana da ita" "To uncle Jauro," Da gudu kuwa ta shiga cikin gida ta shiga dakin su, Mama dake tsakar gida tana fama da uban wanke-wanke na gidan yanda kasan na gidan biki,dan tana zaune Goggo ta shigo wai ta fito tayi wanke-wanke,ya ta iya haka ta fito dole tunda acikin gidan su take zaune,abincin dako Aisha ba'a iya ma tayin shi amma suna sata aiki saboda ta rabe su, Jirjiza kai tayi domin ta hanata gudu amma baji za tayi ba,sai dai Allah ya shirya, Gani tayi sun fito ita da Amina,"ina zaku"ta tambaya,dan har yanzun jikin Amina da zazzabi,shi yasa data nace akan sai ta bata wanke-wanke tayi ta hana ta, Matsowa tayi in da Mama take dan taga yanda ƴan gidan suka wani maida hankali kanta, A hankali ta faɗa mata sakon Jauro,dafe kirji tayi"Allah tasa ba wata magana Sumaiya ta dauko min ba? "In sha Allah ba komai Mama,ai yaron nada hankali bari dai naje naji ko menene? " Shi kenan" Tana fita ta same shi a wani dakali na ƙofar gidan a zaune, Sallamah ta mai "kanina ya ka ke" Da sauri ya Mike tsaye yana nuna mata inda ya tashi"zauna nan Aunty mu" Dan murmushi tayi tana jirjiza kai"A'a ba sai na zauna ba" "Dan Allah ki zauna" Ba yanda ta iya tunda ya haɗa ta da Allah,dole ta zauna, "Ya jikin naki" "Da sauƙi,sosai" Jinjina kan yayi"gaskiya Dahir bai kyauta ba,in sha Allah sai ya gane kuran shi " "Umm" Kawai ta iya cewa. "Aunty Amina dan Allah so nake nayi magana da Mama,amma ban san ta yanda za'ayi ba,tunda gidan naga na jama'a ne," "Haka ne gaskiya kam,sai dai in zaka tsaya a ta cikin zaure sai na mata magana ta fito" "Kina ganin babu damuwa! " Eh babu,bari a mata magana " "To,ina jira,amma har da kema ki dawo pls" "To" Komawa tayi cikin gida ta faɗa ma Mama yanda suka yi,kallon wanke-wanke dake gabanta tayi wanda ko rabi bata yi ba, "Kira Aisha ta zo ta kama,ko ƙanana ne sai ta fara wanke wa" "To Mama bari na ɗauko tabarma" Ta riga Mama fita ta shimfida Tabarma sannan ta mai iso, Yana ganin fitowar Mama ya mike tsaye da sauri,ya shiga gaishe ta bayan sun amsa sallamar ta shida Amina, "Zauna mana Jauro" Komawa yayi ya zauna,yana dukar da kai, "Amina ta faɗa min kana son ganin mu,ina fata lafiya ba Sumaiya ɓace ta dauko min magana" Murmushi yayi jin an kira sunan masoyiyar shi,"A'a Mama babu abinda tayi,tana ma barci na fita" Gani yayi ta dafe kirji tana hamdala,Allah sarki duk sai ta bashi tausayi, "Tun ina da Shekara takwas Allah yama iyaye na rasuwa,bansan daɗin mutum ya tashi da iyayen shi ba,na tashi cikin kewa da kaɗai cin su,ina rokon Allah ya bani mata wacce zata ɗebe min wannan kewar,sai Allah ya shigo da Sumaiya rayuwa ta,Mama ba zan ɓoye maki ba,ina matukar son Sumaiya tamkar rayuwa ta,duk wani abinda zai dame ta ya hana ta farin ciki ba na so, Na roƙe ta akan ko zata yarda nima na zama daya daga cikin Ahalin ta,ta kuma amince min, Mama ina rokon ki bani dama na zama ɗa a gare ki na har abada,bawai Siriki ba"ya faɗa yana dukar da kai, Share hawayen daya zubo mata tayi tana godewa Allah "ni dama tuntuni kallon ɗa na nake maka Jauro,sai da tunda ka roƙi na zama mahaifiya a gare ka,ba zan kiba,domin ɗa na kowa ne,Allah ya maka Albarka,kuma a duk lokacin da kake da bukatar ganin mahaifiyar ka,kazo ka same ni,ka dai na min kallo a matsayin mahaifiyar matar ka,ka kalle ni a matsayin taka mahaifiyar,idan kana da matsala ka zo wurin mahaifiyar ka"ta faɗa ta tabbatar mashi da kalamanta. Shi kanshi da Aunty Amina dake gefe duk hawaye suke"na gode Mama,na gode sosai,Allah ya bar mana ke" "Amin Dana" "Ina kuma mai baku haƙuri,da Jaje akan abun daya daru a jiya,kuma Aunty Amina nima ina bayan ki,ba zaki koma wannan gidan ba,mun gode ma Allah tunda Baban yaran da Kakansu na son su,ba zasu bari wani abu ya same su ba ko ya cutar dasu,in sha Allah zasu rayu babu matsala, Sannan Mama dan Allah ina rokon ki akan karki ce A'a,ko Sumaiya bata San da wannan hukuncin dana yanke ba, A kwai gidan dana siya a Padukwai zaku koma da zama can,na riga na saka an kammala kyara komai na gidan,wanda dama na siya tun last year ne amma ba kowa a ciki, Ina ganin idan kun koma can hankalin ku zai fi kwanciya,Baba ba zai takura maku ba,har balle ke Aunty Amina kina bukatar hutu da kwanciyar hankali,dan Allah Mama karki ce haka a matsayina na ɗan ki " "Tab,lallai Jauro ya iya daure mutum da jijiyoyin jikin shi,yanzun dai baza iya ci masa musu ba" "Kana ganin babu matsala Jauro,bana son fa abunda zai je ya dawo" "Mama in sha Allah babu komai na maki Alkawari" Ajiyar zuciya ta sauke "shi kenan Jauro,yaushe zamu koma" "Ai yanzun haka mota na hanya wanda zai zo ya dauke ku" Duk kallon mamaki take mai"yanzun haka" "Eh Mama," "Gashi Baba baya gida,sai dai zuwa yamma in ya dawo sai na mai bayani,sai mu tafi" "To Mama,dan Allah karki faɗa masa komai,ina nufin karki fada masa ni na bada gida" "In sha Allah mun kuma gode Jauro Allah Ubangiji ya maka Albarka,ya baka zuriya na gari" Sosai yaji daɗin wannan addu'ar nata kafin ya mata sallamah ya wuce. Baba bai dawo ba sai kusan biyar na yamma, Har dakin shi ta shiga ta same shi,gaida shi tayi sannan cikin,ba tare data damu da yanda yake wani haɗe fuska ba,"Baba mun samu gida a unguwar Padukwai zamu koma yau,na gode sosai da karɓa ta da kayi a karo na biyu" "Me yasa zaki kama haya,ko kin manta ba kiɗa gidan da yafi nan ne,ko kuma kin raina dakin da aka baki" "A'a Baba,ba na son na sake jikina ne Alhalin gida na magada ne,ko yaushe suna iya buƙatar abin su,dama kuma ka ce na yi kokarin na koma gidan mijina tunda nan ba ni da gado,shi yasa nake son na bar nan kafin na manta hakan,ƴan kudin dake hannu na nayi amfani na kama mana haya,ina ga hakan zai fi,yanzun zamu tafi dama kai nake jira ka dawo saboda muyi sallamah,na gode Allah ya ƙara lafiya " Gabaɗaya yama rasa me zai ce mata,jikin shi yayi sanyi,domin bai taba sammanin zata tashi nan kusa ba,bai yi sammanin maganar daya faɗa mata tare ke har ya mata ciyon da zata iya maimaita mai ba,tunda take dashi komai munin gorin da zai mata tun tana budurwa har zuwa yanzun bata taba daga kai ta kalle shi sai dai tace to,ko kuma tayi shiru, Yau dai kam jikin shi yayi sanyi,ji yake kamar yace tayi haƙuri ta dawo,sai dai ba zai iya ba,yasan duk in da zata je ba zata yi karko ba dole dai ta dawo gida, "To ita wannan yar taki haka zaki ta yawo da ita da auren ta? " Auren ya mutu tun daga lokacin da ya daga hannu shida Uwar shi suka mata duka,"tana gama fadar haka ta tashi ta fita, A tsakar gidan ta samu mutanen gida tsattaye suna kallon yanda wasu samari biyu ke fitar da kaya, "Goggon ni zan wuce domin mun samu haya a unguwar Padukwai" Amaryar Baba cikin bakin ciki,domin bata so haka ba tace"to yanzun ga wanke-wanke na hada amma sai kin tsaya kin yi min sannan ki tafi ko,tunda dazu kin ma goggo" Bata bata amsa ba sai murmushi da tayi kawai ta kada kanta ta fita rike da hannun Allah yayin da Amina ke binda a baya,tana ƙara gode wa Allah. Babu wanda yace bari ya bi su yaga ina zasu koma,dan haka suna shiga mota mai mota ya ja suka wuce, Gidan bai da nisa da bakin titi,babban Get ne sai Flat guda biyu,sai dai ɗayan ba kowa,daya kuma shine nasu,dakuna uku ne aciki, sai wurin ajiye tarkace,da kicin da kuma dakin zuba abinci wanda babu kalan abinci da babu a ciki,harda jarkan manja dana man kyada, Ɗakunan kuma na Mama yanda kasan dakin amarya,haka na Aunty Amina,ita kanta auta an kyara mata daki daya harda gado da dura irin wanda ake jera takardon karantawa,dakin yara ƴan gayu tsaf,sai tsalle take saman gado tana ihun murna, Gabaɗaya ma ta rasa da wani baki zata saka ma wannan yaro Albarka,har Sujada tayi ta godewa Allah, Dole kayan su a dakin ajiye tarkace suka jibgasu,sai abubuwan buƙata kamar dai kayan sawar su kadai suka cire, Zuwa Magrib kuma sai da wata mata likita ta toro tazo ta yi treatment din Aunty Amina,tare da bata magunguna,ta kuma dauki duk in da ta ji ciwo hoto, sannan tai masu sallamah ta wuce. *🍂JAURO🍂* (MAI ANGUWA) Story & Writing By JIDDARH UMAR 🌟🌙🌙🌙🌙🌙🌙🌟 *🌙✨MOONLIGHT WRITER'S ASSOCIATION🌙✨* https://m.facebook.com/Moonlight-writers-association-109698351308376/ *'''We are the moonlight writers we shine all over the world.''🌍'* ✍️✍️ بِسم الله الرحمن الرحيم ~~~~~~~💞💞~~~~~~~ *Ban yarda wani ko wata su saka min littafi a shafin su ko su mai da min littafi Audio ba tare da izini na ba* *55* *Wannan littafin nawa mai suna a sama na mai da shi na kuɗi,tare da Yar Tsanar Zinare,wanda yake son guda ɗaya dari uku 300,guda biyu 500 dari biyar, Hauwa Umar,Zenith Bank,2284905309,sai shaidar biyi ta wannan number 08141644865* Yana barin Limawa komawa gida yayi zuciyar shi cike da tunanin gimbiyar, Ganin bata falo ne yasa kai tsaye ya shiga dakin ta,tana zaune kan darduma tana faman danna waya, Rungumeta yayi ta baya yana sumbatar kumatunta,"barka da rana Baby" Kin kulashi tayi,sai ma kauda kai da tayi"sai dai kace barka da yamma" "Allah ya huce zuciyar Baby Sumy,nasan nayi laifi a tausaya Amin haƙuri,kin san wani abu kuwa?duk in da nake ina ta tunanin ki,ina ta missing din ki" Ƙara bata rai tayi tana juyowa"ba wani,amma shine ko dan test Massage bata turo minba,ka barni ni kaɗai a gida inata jiran ka"duka ta kai mai kaɗan a kafaɗa cikin shagwaba tace"you're not romantic Jauro" Dariya yayi yana rike hannun nata tare da sumbatar shi,"worry not,i will try my positive best to be a romantic husband"ya faɗa yana jawo ta jikin shi,ya haɗe bakinsu wuri ɗaya,cikin kwanciyar hankali da dubara ya fara tafiyar da ita,dan baya son ta tsorata, Cikin sanin lagon mace ya gama riki ta mata lissafi,ya mantar da ita duk wani fushi da ɓacin rai da take yi, Ɗaukarta yayi ya kwanta da ita kan gado,yana hayewa kanta, Kamin wani lokaci bakajin sautin komai adakin sai saukar nimfashin su, Bayan wani ɗan lokaci na kuma lekawa ɗakin,dan ni kan basu wuri nayi, Lullube suke a cikin zanin gado,tana wance a jikin shi,idanun ta a lumshe, Shafa fuskarta yayi"kar kiyi bacci,tashi muyi wanka" Ƙara runguneshi tayi,cikin kasala tace"ba zan iya tashi ba,ka riga ka kararmin da ruwan jiki na" Shafa suman kanta yake"da badan kin nime dana ƙyale ki haka ba,da sai na saka kin releasing sau huɗu,amma gashi tun kan aje ko ina kinyi biyu kina fadin ruwan jikin ki ya kare a romance kawai,to ina ga in na shiga asalin maji daɗi" "Ina ne kuma Maji daɗi? Cinyarta ya fara shafawa yana yin sama da hannun shi" Bari na nuna maki hanyar" Da sauri ta rike hannun nashi tana buɗe idanun ta,"na lura kasan salon yanda zaka saka sha'awar mutum ya tashi badan ya shirya ba,ni dai karka karamin da ruwan jiki,tun kan aje ko ina" "Umm Baby Sumy don't be a Cry Baby,in dai kina tare da ni ruwan jikin ki ba zai taba karewa ba,sai dai ma ya ƙaru" "Kace kai Vigin ne ta yaya kasan irin waɗannan abubuwan," Ta faɗa tana tsare shi da ido, Dariyama ta bashi,wato tuhumar shi take yi, "Ina fata baka taba Practical da wata ba ko? Dan kanne ido yayi" I wonder why mu maza idan muka ce mu Vigin ne ba'a yarda,ina ga zamu fara zuwa awo a asibiti domin a dunga tabbatar wa" "To me yasa baka fada min da wuri ba? " Me kenan"ya tambaya, "Batun zuwa awo,ai dana kai ka an duba min kai,dan irin wannan abun da kake yi kamar wanda ya gama sanin komai" Dariya yayi yana ɗaukar ta gaba ɗaya suka shige bayi"karki manta Mijinki likita ne,in dai akan macce ce zan iya maki cikakken discribing ɗin ta,na kuma haɗa maki da Anatomy and Physiology,naku na mata,kin ga duk wani kafa,ko lungu ko jijiyar da zai tada maki sha'awa na sani,shi yasa nace ki kwantar da hankalin ki"ya faɗa yana saka ta cikin ruwan dumin daya haɗa masu, "Amma this is not fear,kai kasan nawa,ni bansan naka ba,ni ma ka koyamin na maza,' " Saboda ne" "Saboda kaima kasan na mata,kaga idan kamin sai na rama,in ba haka ba cutata kawai zaka rinyi" Dariya ya fara saboda a irin yanayin data kare maganar harda murguda mai baki, "Sai dai ki koya sanin na mijinki da kanki" Zaro ido tayi"ta yaya zan sani" "Zaki sani amma a hankali" Zata ƙara magana ne ya daura ɗan yatsarshi saman lebenta "babu kyau magana acikin banɗaki,ya faɗa yana jawo ta jikin shi bayan shima ya zauna cikin ruwan. *BAYAN SATI ƊAYA* A zaman da tayi tare dashi ne ta fahimci asalin waye shi, Mutum mai sauƙin kai,iya soyayya,tarairaiya,kula,haƙuri,girmamawa, tausayi,gabaɗaya acikin abunda ta lissafo babu wanda bata gani ba a cikin sati daya,domin hutu ya ɗauka na sati ɗaya a wurin aiki, Acikin satin daya da sukayi tare,bai wuce sau biyar daya kusance taba,bawai kuma dan bashi da lafiya ba,ko yana dauke da wata matsalar,A'a kawai dai ta lura komai shi yana yinshi ne a cikin tsari da taka-tsantsan,domin cewa yayi yawan kusantar mace yana sakawa ta ji abun ya fita ranta,ko kuma tai ta jin haushin ka,ko kuma ka gundireta,yana kuma saurin tsufar da mace, Sai yasa yawancin lokuta yafi bada ƙarfi wurin romancing ɗin ta, Ta bangaren abinci kuwa,baya bari taci abincin banza,ina nufin ba mai kara ni'ima da kuzari ba,ya Daura ta akan Balance Diet,dan yace baya son nan da shekaru tana yarinya karama,ta buɗe ta zama uwar mata, Shi mutum ne mai saurin sake jiki,har balle idan ka fahimce shi, Yawancin aikin gida tare suke yi,wani lokaci ma tana barci kafin ta tashi har yayi shara yayi wanke-wanke,ya haɗa masu abin kari, Haka girkin rana ko na dare,zai ce ta zauna bari shi yayi,baya jin kyashin yi mata komai, Wani lokaci idan suna zaune suna kallo ko suna hira,zai tashi da kanshi ya shiga kicin ya yanka fruit a plete ya kawo masu,ko kuma in yana buƙatar abu sai ya tashi ya dauko ya dawo, Takan ce "Jauro me yasa baka cewa na ɗauko maka,ko na maka kamar yanda sauran mazaje ke yi" Sai dai yayi dariya yace"lokacin da ban aure ki ba wake min?duk ni nake yi da kai na,to me yasa yanzun don na same ki sai na sakar maki komai nawa nace ke zaki yi,harda abinda bai taka kara ya karye ba?kin ga ni ba haka nake ba,na aure ki ne kawai ɗan ina son ki bawai dan in mai da ke ƴar aiki na ba,kyanki da kyan jikin ki yana daya daga cikin abinda ke ƙara min ƙaunar ki,yake saka ni nishaɗi,to me yasa ba zan yi tattalin su ba,zan bari ya lalace,,shi yasa kika ga ina mentening ɗinki,ta yanda ba zaki lalace ba,ta yanda zaki dinga samun isasshen hutu,so ki kwantar da hankalin ki,hakan ra'ayi na ne" Tasowa tayi daga in da take tazo ta rungume ta,tare da bashi light Kiss "you're so romantic Hayati" Dariya yayi "kin tabbata" "Sosai ma" "To karki damu I will always be romantic husband for you my dear" "Thank you" To haka rayuwar su ke tafiya cikin farin ciki,sai dai matsalarta daya dashi,shine yaki yarda ya kaita ta kara dubo jikin Aunty Amina,sai dai su yi waya, Su kuma har yanzun ba wanda ya faɗa mata cewa Jauro ya basu gida,dan daga baya ma ya dauki takardar gidan gaba ɗaya ya danƙa ma Mama wanda aka mai da shi da sunan ta, Kullum sai yaje gidan sun sha hira da Mama,amma bai taba faɗa mata ba. _______ta bangare Baba kuwa al'amura ne suka dagule mashi tsakanin shi da Maman momy,domin kiri_kiri bai isa ya taɓata ba,saboda irin zafin da dukkan su suke fuskanta,ko kusa da ita bai son matsawa,saboda hucin dake tunkaro shi, Matsalar da aka samu kuma shine bawai iya shi bane idan ya taɓa ta take jin zafi,a'a haka kawai za ta ji jikinta kamar ana hura mata wuta saboda zafi,idan kuma tace a taba jikin ta aji,sai dai aji sanyi har wani zufa take,amma a ciki ita tasan abinda take fuskanta, Da Azaba yayi Azaba,zafin duniya ya ishe ta ne,yasa da kanta ta fara faɗin abinda ta aikata mai,lokacin yana wurin aiki Momy ta kirashi tana kuka tace yazo gida jikin maman su ya riki ce,sai wasu maganganu take faɗa wanda bata gane ba,dan Allah yazo, Cikin gaggawa kuwa sai gashi ya dawo, Tana kwance kan gado sai mulmula take kan gado tana ihun a taimaka a cire mata kayan jikinta zafi zai hallakata,ita zafi take ji,zata mutu, Dan Momy ne da wata kawar Maman su data kira wato Aminiyar mamanta,Aunty Abigirl, suka danne ta suka hana ta cure kaya. Kiran sunan ta yayi "Maman Momy" Ya faɗa yana tsaye a bakin kofar dakin,dan bai iya shiga, A gigice ta juyo"yauwa,yauwa,Kazo,to sannu da zuwa,dama kamar kasan ina nimanka "ta faɗa cikin fitar hankali,wanda kai kanka daka ganta kasan ba'a cikin haiyacinta take ba, " Kasan wani abu kuwa,lokacin daka nuna kana so na a wancan lokacin naji daɗi sosai,domin nasan idan na aureka duk wani yangan da Maman Sumaiya ke mana ya kare,domin duk abinda ka bata dole zaka bani,sai kuma naji dadi daka nuna baka son matarka ta sani saboda kawata ce,tare muka tashi,ni kuma na yarda,in faɗa maka lokacin da auren mu ya rage saura sati ɗaya har gida naje na same tana zage ta sosai,nace mata zan aure mijin da take takama dashi,naci mata mutunci saboda ta tayarda hankalin ta,sai dai ita ko a jikinta,duk da na tabbatar da hankalin ta ya tashi,tayi kuka sosai,sai dai taki nuna maka ta sani har sanda ka aure ni,bata taba nuna ta san kana da wata mata ba,har gida na sha binta in mata cin mutunci,amma bata kula ni, Gabaɗaya haushi take bani,na tsani in ga farin ciki a fuskarta,ganin ta samu cikin Sumaiya har ya kai wata bakwai ni kuma ban samu ba,yasa na koma ma tsohon saurayina muna mu'amala tare,har ba samu ciki, Saboda kana da son zuciya shi yasa naje muka maka Asiri ni da Mama ta,akan na mallake ka,kuma boka ya tabbatar min abu ne sauki ne dan kai ma bawai sonta kake sosai ba,kafi sona,kuma kanada son zuciya,shiyasa cikin sauki komai ya kamaka, Naso ace namiji na haifa,amma sai gashi na haifi mace, Na saka ka maida ni sabon gida ita kuma ka barta a tsoho,Alhalin gidan harda kudin ta aka cika aka siya fili aka kuma yi gini,amma bata taba kula kaba, Dana yaye Momy sai na canja saurayi wanda bamu daɗe dashi ba,to dashi ne na samu cikin junior,na kuma haifeshi,"fashewa tayi da dariyar mugunta "kai kuma sai wani murna kake yi akan an haifa maka Namiji,Wawa kawai,harda wulakanta matar ka,ni kuma ina ta jin daɗi, Na saka yan uwankan sun tsaneta,sannan na saka ka zaba ma yarta Amina miji mara mutunci mai dukanta,wanda duk lokacin data gudo gida gan niman taimako sai na saka kaci mata mutunci ita da uwarta ka kuma korata,wannan yasa ta tsaneka,ita kuma mara kunyar Sumaiya na haɗa ta da ɗan ƙauye wanda matsalar dangin su kaɗai ya ishe ta,itama na saka ta sane ka,bayan na je gidan boka na masu Asiri ta yanda idan mijin ta ya taɓa ta zai dinga jin zafi kamar ya ƙone,irin dai yanda nake ji,ita kuma na saka mata sha'awa ta yanda zata bi maza, Dama boka ya faɗa min idan Asiri ya karye zai dawo kai na, Ni na zuga Uwar mijin Amina ta tsane ta,sannan nake saka tabin bayan ɗan ta,shi yasa taimata duka ita da ɗanta, Kai kuma daga karshe na saka ka karubutawa matarka saki day_daya har uku da hannun ka,ni kam ko yanzun na mutu na cika buri na,naji daɗi na raba ka da ita har abada"ta faɗa tana kyalkyacewa da dariya,sai kuma ta saka ihu tana fisge_fisge,kafin ta arta da gudu har ta bangaje shi ta fita gidan da gudu, Gabaɗaya gidan yayi shiru baka jin komai sai kukan Momy dake faɗin "Mama Allah ya isa tsakanin mu dake,kin cutar da rayuwar mu" Tana faɗa tana kunjin kuka,yayin da ita kuma Aunty Abigirl tayi shiru kamar ruwa ya cita,dan duk mugun halinta bata taba tsakanin Maman Momy ta fita ba,sai gashi yau taji abinda yafi ƙarfinta, Zamewa yayi anan bakin kofa in da ta tureshi ya faɗi,zaman yan Bori yayi yayinda gudun zuciyar shi ke ƙaruwa, Tun daga farkon Al'amarin ya fara tariyowa a ƙwaƙwalwar shi, tabbas ya nuna zalamarshi da son zuciyar shi,shi mutum ne mai son zuciya wanda hakan ne ya jawo mai komai,gashi sanadin haka ya rabu da matar shi da yayanshi,da su ka tsane shi, Macen kirki,wacce duk abinda zai mata bata kula shi,idan har bai dawo da ita rayuwar shi ba yayi Asara,ga ya'yan daya nuna mason duniya ashe ba nashi bane,nashi ya wulakanta rayuwar su, Mikewa yayi da sauri zai wuce, Cikin gigita Momy ta taso ta rike ƙafar shi "Baba! Baba! Ina zaka tafi ka barni,dan Allah ka tafi dani karka barni! Ni ba ni da wani uba daya wuce kai,kai ne Baba na,dan Allah karka tafi ka barni,bansan yanda zan yi da rayuwata ba ka taimaka min Baba" Ji yake tamkar ya hambaran da ita ya wuce,saboda duk ta sanadiyar su da uwar su komai ya ruguje,ya tarwatsa rayuwar yayanshi,duk da yasan ba laifinta bane ita ma yanzun take sani,amma a wurin shi amsar ta ba abu mai sauƙi bane,idan kuma ya wuce tamkar ya zama mai son kai ɗin ne,dan haka ya danne zuciyar shi ya tsugunna ya dago ta"karki damu har a bada ke yata ce,ba zan taba gudu na barki ba,ki zauna tare da Aunty Abigirl,ko kuma ki bita gida zange na dawo ne,zan zo na ɗauke ki" "Ka tabbata zaka dawo" "Na maki Alkawari,sannan ki kira gidan Kaka ki faɗa masu halin da Maman ki ke ciki" Tana kuka ta tashi ta koma cikin dakin ta rungume Aunty Abigirl. Fita yayi ya hau saman mashin dinshi ya tayar,yasan wuri ɗaya zai same ta,shine a Unguwar Limawa gidan Babanta, Dan haka kai tsaye can ya nufa, Ko da ya isa a ƙofar gida ya samu Baba zaune,da sauran abokan shi suna hira, Da kyar ya iya sai saita kanshi ya gaida su, Baba ne yace"Baban Aisha ya na ganka haka kamar a rikice"kasancewar sunan babban danshi gare shi shiyasa baya kiran sunan shi, Dukar da kai yayi cikin jin nauyi yace"Baba nazo ne wurin Maman Sumaiya,ko tana ciki? Ya karasa faɗa da tambaya, "Ai bata gidan nan,yau kusan sati ɗaya kenan,domin kuwa tazo ta same ni akan ta kama haya a can wani unguwa zata koma ita da yara,shine fa ta tafi" Gaban shine ya rinka faɗuwa,ba dai ta bar garin ba,to ina zata tafi,ji yake zufa na keto mai, "Amma lafiya kake niman ta,ina ce ka rubuta mata saki sannan ka ce ka bar mata ya'yan,? " Baba wani babban Al'amari ne ya faru,dani a yau ɗin nan,"nan ya shiga basu labarin duk abinda ya faru,yana yi yana sharan hawaye,, Gabaɗaya wurin yayi shiru,kowa tsoron Allah na ƙaruwa a cikin zuciyar shi,wannan wani irin rashin imani ne, Daya daga cikin tsofaffin dake zaune ne yace"tabbas idan ɓera da sata to daddawa da wuri,kai ne babban me laifi,domin tun farko idan da Ace ka tsaya ma gaskiyar ka akan wannan Al'amarin da hakan bai kasancewa,kamar yanda kowa ya sani matarka ba mai matsala bace,macen kirki mai haƙuri,na tabbatar koda ka faɗa mata niyarka akan kawar ta ba zata ki ba,idan da ka girmama matarka da waccen Arniyar bata isa ta wulakanta taba,amma gaba ɗaya ka dauki hanyar rashin gaskiya,ka ci amanar ta,ta sani amma bata nuna maka komai ba ta barka da halinka,ka ƙuntata mata ita da ya'yan ta,yanzun wa gari ya waya,sai kai,wake nadama,sai kai,idan da ace ka rike gaskiya duk abinda ita waccen zata maka dan ta shiga tsakanin ka da matar ka da yazo da sauƙi,ba ace Asiri karya bane,Asiri gaskiya ne tunda yaci Annabi,amma idan ka kiyaye Allah da dokokin sa,shima sai ya kiyaye ka,idan ya tashi saukar maka da fitina sai ya zo maka da sauƙi,shi yasa yake da kyau duk rintsi duk wuya bawa ya kasance mai tsayawa akan gaskiyar shi,ka rike gaskiya,sai ka zama abin girmamawa,idan kuma ka rike karya sai ka zama abin kwatance,Allah ya rabamu da aikin dana sani " Dukkanin su da Amin suka amsa, Cikin zubar da hawaye yace"Baba yanzun babu yanda za'ayi a mai da mana da auren mu? Murmushi tsohon yayi"sai dai ka yi haƙuri Allah ya ƙadarta iya wa'adin zaman da za ku yi tare da ita kenan,amma babu wata hanyar,shi yasa babu kyau ko kaɗan irin wannan sakin a Musulunci,ka saki mace saki uku ras,to wallahi sai Allah ya jarabceku,idan kai ne ka yi da sanin ka,idan kuma ita ce ta saka kayi,Ubangiji ba zai kyale ku ba,dan awanan lokacin zaka ji wani irin sonta na taso maka na matsifa,haka idan itace,ka sani Allah shi ya halarta mana yin saki,amma kuma a duk lokacin da akayi ta,sai sama da kasa sun girgiza,mu yan Adam bamu San komai ba,har balle mu da muka kasance masu matukar sakaci ta ko wani fanni,dan haka sai dai ka yi hakuri,sai kuma in Allah yayi da rabon zaku sake zama shi ne bamu sani ba," Ya fahimci me yake nufi sosai tunda shi ba jahili bane amma kuma son zuciya yasa yayi aiki irin na jahilai,gashi kuma yanzun ji yake tamkar ya jawota su koma gidan su, Share hawayen da suka ki daina tsayawa yayi"Baba ina son in je in nime tafiyarta,sannan kudin hayar da suke ciki,zan dinga biya ko dan yara na," Jinjina kai yayi"ba kai kaɗai ba,ni kai na zan so naje na nime yafiyarta akan abubuwan dana ta yi mata saboda ba ta da shi,ɗan uwana ya rasu ya barmin amanarta amma haka nata wulakanta ta,na gode ma Allah daya buɗe min ido tun yanzun ba sai da ƙasa ta rufe min ido na haɗu da dan uwana,na kasa bashi amsa ba," Duk na'am suka yi da maganar su,"Baba yanzun wani unguwa take" Dan shiru yayi yana nazari kafin yace"kaga kuma sunan unguwar ya ɓace min,yama sunan unguwar nan na bayan Kasuwa" "Wani kasu kenan? " Kure market,ina nufin sabon kasuwa" "Kodai Padukwai"daya daga cikin tsofaffin wurin ya faɗa. " Yauwa can,anan ta faɗa min,wai gidan bai da nisa da bakin titi" Sawa yayi aka kira mai babban ɗan shi,sai kuma shi Baba ya zama su uku suka tafi. Da kyar da tambaya suka gane gidan,da fari sun yi tunanin ba gidan bane saboda ganin irin girman shi,sai dai suka ce bari su tambaya, Suna sallamah kuwa sai gashi Aisha ce ta buɗe masu Get, Ganin fuskokin waɗanda ke tsaye ne yasa ta tsaya cikin mamaki tana kallon su,kafin ta kira sunan Baban ta"Baba me kazo yi nan,ba mun bar maka gidan ka ba,ai nan gidan muna yanzun" Duk kallon mamaki suke ma Aisha yarinya karama shekara takwas ta san ta faɗi haka,ko da yake ba laifinta bane ga mai laifi nan tsaye tunda shine idan ya tashi ci ma uwarta mutunci baya duba idon yarinya,Alhalin su yara basa mantuwa,shi yasa bai da kyau idan faɗa ya haɗa ma'aurata suyi shi a gaban ya'yansu,domin yaran zasu girma ne da abun acikin zuciyar su,kamar dai Aisha,gashi kiri_kiri take faɗa masa ba gidan shi bane. Jawota yayi jikin shi ya rungume ta"ki yi hakuri Aisha,na sani,ba nazo koranku bane,nazo ne niman yafiyar ku,kai ni wurin maman ki" Bata ce masa komai ba sai zame jikinta da tayi a na shi tayi gaba suna biye da ita a baya,har ta buɗe ƙofar ta shiga, Ganin sun tsaya ne tace "ku shigo sai na kira Mama" Bin bayan ta suka yi,sai dai suna shiga suka sake baki wurin kallon hadadden falo, Manya kujerun zama tima_tima waɗanda suka kusa cika falon,kai ko TV su ma na bango abin kallo ne,idan ka yi wasa ko silin da wutar da aka kawata falon dashi zai iya dauke hankalin ka, To ko dai nan gidan da take aiki ne, Su dai sunyi shahada sun zauna amma kansu ya kasa tsayuwa wuri daya, Suna zaune sai ga Amina ta fito daga wata kofa sanye da doguwar riga,ta yi kyau ta ciko kamar ba ita ba,ciyon fuskarta kaɗan ya rage ya gama ɓacewa, Babu wani sakin fuska ta gaida su ta shiga kicin ta dauko limun kwali a tire da kofuna ta ajiye a gabansu,ganin da gaske ƙoƙarin tafiya take kamar wacce bata sansuba yasa yace"Amina baki ganni ba" Kafin ta basu amsa ne suka ji wani ni'imtaccen kamshi turare kafin taku ya biyo baya,sanye take da hijabi iya guiwa,sai Atamfa riga da zani wanda zanin ne kawai kake iya gani,dai kuma takalmin ta da yake zubin silifas amma mai kyau, Yanda kasan ba ita ba,ta kara ƙiba da cikowa har wani haske ta ƙara,na kwanciyar hankali, Da kallo suke binta har ta iso ta zauna kan daya daga cikin kushin, Kallon su take cikin kwanciyar hankali,babu wani firgita ko mamaki,"Baba ina wuni," Da kyar ya iya amsawa har bakin shi na rawa, Kafin suma ta hada cikin jam'i ta gaida su,wato da yayanta da shi uban gaiyar, A sulake suka amsa, "Baba da fatan lafiya na ganku da rana tsaka? Sun ma rasa ta ina zasu fara bayayi,dan kowa jikinshi yayi sanyi,domin a yanayin da sukayi sammanin zasu same ta,sai abin ya juya, Shine dai ya ɗaure ya fara magana" Dan Allah ina niman Alfarma ko zaki kira mijin Sumaiya kice ya kawo ta ina son ganin ta,dan nafi son na fara magana a gaban kowa" "Kai me zai hana ka kira shi da kanka" Dukar da kai yayi,cikin jin kunya domin ko number Jauro bai da shi, A hankali yace"dan Allah " Mamaki ne ya kamata,yau shine da ce mata dan Allah cikin kwantar da murya,to Allah ya mata tsari dashi da abinda suke tafe dashi, Kallon Amina tayi",kiramin yayanki kice yazo shida Sumaiya'" Da to ta amsa, Tashi tayi tace"zan koma ciki idan sun iso zan fito" Ba wanda ya iya ce mata komai da kallo kawai suka bita, Bayan mintuna ishirin da uku,sai gasu sun iso,ita kanta Sumaiya kallon gidan take,domin be faɗa mata inda zasu ba, Ganin mutane dake zaune a falo da Aisha dake wasa yasa ta fara tsorata kardai ace Mama ce ta mutu,da sauri tayi wurin Amina a tsorace,"ina Mama" Riƙo hannun ta tayi suka bar Jauro a falo shida su Baba, "Ke ki natsu tana daki" "Lafiyar ta kalau dai? Tura ƙofar tayi suka shiga,da gudu ta fisge hannun ta cikin na Amina ta rungume Mama tana sauke ajiyar zuciya" Mama har naji tsoro,meke faruwa,nan kuma ina ne" Zaunar da ita tayi"ki natsu,nan gidan mu ne" Ƙara kallon dakin take"gidan ku kuma? Ajiyar zuciya Mama ta sauke,sannan ta shiga ba ta labarin duk abinda ya faru tsakanin ta da Jauro har yau da zuwan Baban su,"Sumaiya mijin ki ɗan Albarka ne,dan Allah ki rike shi da zuciya daya,ki kyautata mai kamar yanda ya ke kyautata min,babu ranar da bai zuwa dan duba lafiya ta," Cikin tsananin mamaki tace"amma Mama bai taba fada min ba,wani lokaci har kuka nake masa akan ya kawoni na duba lafiyar ku amma sai yaki" "Shi yace kar a faɗa maki,kinga harda takardun gidan duk ya mallaka ma Mama" Cewar Amina, Kukan farin ciki ta fashe dashi tana rungume Aunty Amina "na gode_na gode" Ture ta tayi suna mata dariya ita da Mama "mijinki zaki je ki rungume ki masa godiya ba ni ba" Aisha ce ta shigo tace"Mama ana magana a falo" Tare suka fita dukansu, Kallon Mama Baba yayi kafin ya fara bata labarin duk abinda ya faru,yana yi yana kuka tare da nuna tsantsan ladamarshi,gashi babu damar maida ita ya riga tayi barna,ya cuce rayuwar shi, Baba ma ya Daura ya bada nashi haƙurin har da cewa ta bar aikin da take yi,ta zo ta koma gida zai bata babban daki kuma za'a dunga zuba mata abinci ita da yaranta, Baban Aisha ne yace"in kuma baƙi son komawa ni zan dinga biyan kudin haya dana karatun Aisha har da na Abincin ku duk wata" Murmushi tayi tana godewa Allah daya nuna mata wannan ranar a rayuwar ta, "Ni Bani da abin da zan faɗa sai dai in ce Alhamdulillah,domin yanzun bana cikin kunci da tashin hankali,ina cikin farin ciki ni da yara na,wannan gidan da kuke gani ba aiki nake yiba,gidanane mallakina,wanda ɗan da Allah bai Bani ba a baya ya Bani yanzun,wato Jauro,a lokacin da nike tsaka da niman taimakon wadanda nake tunanin zan iya jingina da su,suka juya min baya,sai gashi Allah ya kawo mun shi,ya gama min komai,ya saka ni farin ciki,ya siyamin gida,ya Bani abinci,yana kula da ya'ya na,yanzun haka yasa mijin Amina ya bada takardar ta makaranta zata koma,dan haka idan nace na kullace ku kamar ban gode ma Allah bane,ni na yafe maku duniya da lahira,komai ya wuce,suma kuma yayana sun yafe maka domin kullun cikin yi masu nasiha nake,Amina ku faɗa ma babanku" Duk jikinsu sanyi ya kara yi, "Baba mun yafe maka" Suka haɗa baki wurin fada,domin yafe mashi babu abinda rai kara masu koya rage masu,haka kuma rashin yafe mashi,sai dai ma yasa suta rike abu a zuciyar su, Kuka ya fashe dashi,yana fadin"na cuce kaina son zuciya ya kai ni ga aikin dana sani"haka dai suka ta kwantar mai da hankali kafin su wuce, Tana ganin sun bar falon ta tashi da sauri ta rungume shi tana fashewa da kuka tare da dukanshi a kirji,dariya ya fara to me kuma na kuka" "Shine baka faɗa min ba" "Ba komai bane dan ɗa yama mahaifiyarshi sai ya faɗa" Ranar a gida ta yini sai dare yazo suka sha hira tare kafin su koma gida, _____a bangaren ƙauye kuwa,ƴan sanda sun samu nasaran kama yaran Baffa Bube,Bakari da Ɗan Fodio,waɗanda ake ma zargin yin Kidnapped, Ranar Uwar su kamar tayi hauka, Dama ita rayuwa haka take,wani idan ya canja wani ba zai taba canjawa ba sai dai ya mutu da halin shi,ko mai kyau ko mara kyau,Allah dai yasa mu cika da imani, Amma kam su Ahalin Jauro halin su na nan yanda take,kwana biyu idan abin yayi sauki,idan kuma ta juyo sai hamdala,haka suke tasu rayuwar, Sumaiya kuma ba ko yaushe suke zuwa ƙauye ba,sai lokaci-lokaci yake kaita,sun san halinta,duk girmanka idan kai mata abinda hankali bai ɗauka ba yanzun zata gwada maka nata kalar haukan, Kamar kuma yanda Jauro ya faɗa ya samar mata aikin koyarwa a makarantar secondary School,a nan unguwar su, Rayuwar su suke cikin tsananin soyayya da kwanciyar hankali, Sai da tayi wata biyar a gidan shi kafin Allah ya bata ciki,ranar murna a wurin Jauro ba'a magana,duk wani masoyin shi sai da ya faɗa mashi, Cikin ta naɗa wata takwas aka nada shi a matsayin Ministar of Health,na Niger State gaba ɗaya,Al'amarin daya faranta zuciyar masoyan shi, Mama kuwa yanzun a danginta har wani girma na musamman ake bata,duk in da ta shiga,wanda ita kallon kowa take yi kar da kar, Su Momy kuma idan sun samu hutu Baba yakan kawo su wurin Mama su mata hutu dan bata zubar dasu ba, Yayin data bangaren Mama Momy ta shiga duniya ba'a masan in da take ba, Cikin hukuncin Ubangiji Allah ya sauke Sumaiya lafiya inda ta haifi ƴan tagwage duka maza, Daya yaci sunan Baban shi Jauro,wato Abdul-Aziz,daya kuma Abdul Hakim, Sai dai muce Allah ya raya,ya kuma shiryar damu akan hanya madaidaiciya. *Alhamdulillah* To masu karatu anan na kawo karshen wannan littafin nawa mai suna Jauro, *Sai kuma idan Allah ya nufa FITILAR DARE,zata haska mana hanya domin yin WATA TAFIYAR,tare da SARDAUNA,sai mu haɗe da JAURO domin dauko maku ƳAR TSANAR ZINARI,bayan Sallah idan Allah ya kaimu rai da lafiya*