Sno🌟⭐ *Imaan* ⭐🌟 _By Khaleesat Haiydar_ ✍🏻 *All thanks to Allah SWT for giving me the chance, privilege and ability to start this book, my special greetings goes to my lovely mum Hajiya Hajara and my sweet aunties (Small mums) my siblings aren't excluded also... I love them all, Ban mance ki ba Mama dutse ina gaisuwa da fatan anyi sllh lafiya Allah ya amshi ibadunmu, Hajiya Asabe kema ina gaida ki sosai da maki fatan alkhairi Allah ya raya xuri'a, Hafsat Oum Ilham I greet you too with respect, and My Sophiee I know you won't see this but get this.. jiddo Love's you dear, Lovely fans ina maku fatan alkhairi da fatan gamawa da iyaye lafiya* 1..... Babban compound ne sosai dake dauke da shuke shuke da bishiyoyi masu daukar hankali, kai kana ganin tsakar gidan kasan naira ta xauna, makeken tsakar gidan na dauke da sassa har uku masu fenti iri daya, ko wani sassa kuma akwai tazara mai tsayi tsakaninsa da wani sassan, sashin farko wanda shi xaka ci karo da bayan shigowar ka gate din xamanin dake babban gidan ba dai girma ba don sashin duk ya fi sauran girma, duplex ne babban gaske sai parking space gari guda dake gefe. Durkushe a bakin tap dake babban sashin farko wata farar budurwa ce da baxata wuce shekaru sha takwas ba, duk da a duke take hakan baxai sa aki gane doguwa ce ita din ba, ruwan tap din na ta xuba bucket din da ta tara don ya cika, sai shafa socks din hannunta take kamar mai tausayinsa, daga ves, huluna sai socks kala uku sune kayan da take wankewa a wajen amma ta kusa awa daya, kofar entrance da ta ji an bude ya sa ta kamewa daga inda take durkushe lkci daya ta xaro ido gabanta ya fadi don ita dai a iya saninta babu kowa sashin banda ita da ke wanki tun daxu, occupant din bangaren duk sun tafi biki ta kuma ga fitarsu, wanda da ace suna nan tasan ko hauka take baxata fara xuwa bangaren su tayi wanki ba, a hankali ta juya don ganin wanda ya fito, wani matashi ne dogo sosai wanda baxai haura shekaru talatin da uku ba tsaye dai dai entrance din shiga gidan sanye da jallabiya milk color, Ta dauke kai tana ci gaba da daurayenta, ya rungume hannuwan sa calmly yace "Keee" kamar xata yi kuka ta juya ta kallesa, yace "Me ya kawo ki wanki nan?" Ta buda manyan idanuwanta tace "Tap din mu fa ne ya lalace jiya kuma....." Ya katse ta yace "Tashi ki bar wajen" Tace "To ai na kusa gamawa fa" strictly yana d'an daga murya yace "Kwashe kayan ki ki bar nan kar ki yarda in iso inda kike" ta dauke kai hade da turo baki ta mike ta xubda ruwan gaba daya ta hade buckets din bayan ta xuba yan kayan da ta wanke ciki ta kwashesu gaba daya ta bar wajen kamar xata tashi sama ba tare da ta sake kallon inda yake ba, ta murguda baki bayan tayi nisa, murya can kasa tace "Allah ya isa" Dai dai part na biyu da ya kasance wani babban hadadden Bungalow ta tsaya, shi ma kuma bangaren na da nasa parking lot din da xai dau motoci uku, ta dinga kallon sauran kayan da bata gama wankewa ba kamar xata yi kuka, to ita yanxu ya xata yi da su, Ammi na ganin bata gama ba sai ta fara mata fada yanxu tace tun daxu me take, kallon hanyar da xata bi xuwa part din karshe tayi, ta tabe baki sanin ba lallai ma mai sashin ta bar ta ta ta6a mata tap ba, tana ta tsaye can kuma dai ta wuce can bangaren karshen, shi ma sashin bungalow ne sai dai bai kai nasu ba, tsarin ma ba iri daya bane, a hankali ta ajiye buckets din hannunta dai dai tap din dake opposite entrance din shiga parlor tana yi tana satan kallon kofar, cikin dubara ta bude tap din yanda xuban ruwan bazai yi kara ba, ta tara bucket din a karkace kar ma aji xuban ruwa ta ci gaba da daurayenta, sosai gabanta ya fadi jin taku duk a tunaninta mai bangaren ce, mutumin daxu ne ke tahowa bata yarda sun hada ido ba ta ci gaba da wankinta, ko kallon inda take shi ma bai yi ba, bai kuma kai ga shiga parlon ba suka ji muryar wata tsohuwa tana cewa "Ni wai ya nake jin kamar ana taba min pampo a wajen nan ne" da sauri ta kashe tap din ruwan xata kwashi kayanta ta gudu sai ga tsohuwar ta fito, Sake baki tayi tana kallon ta kafin tace "Waye kuma wannan, meye kike min kusa da pampo?" Budurwar ta turo baki tace "To inna namu ya lalace..." Inna ta katse ta da sauri tace "Da ya lalace ni na lalata maku?" Budurwar tace "To wai ma ba daxu kika ce in xo in debo maki ruwa in kai maki bayi ba, shine fa na zo xuba maki" Inna na mata wani kallo tace "Ke din? Ke din da na sani ce xaki kai min ruwa bayi munafuka? bayan ba Aisha sunana ba, to wllh ki kiyaye ni a gidan nan ruwana ba na banxa bane kar ki sake xuwa min nan, kin lalata naku nima ki xo ki lalata min nawa saboda mugunta koh, to uwar ki ce xata debo mun ruwan idan na tankin ya kare, haka kawai ki bar ni da diddigin pampo duk tsutsa cuta ta kama ni in bar 'ya yana da wahala, ke dai wannan yarinya ta Bukar muguwa ce wllh, shegen barnar ki ta fi karfin ki, to wane 6era ma" ita dai Budurwar sai kallon ta take kamar xata yi kuka, inna na xaro ido tace "Maxa dau min ruwana ki tafi ki juye min a bandaki, ni dai a gidan nan duk wanda ya diba da hakkina gaskiya ban yafe ba tunda abun haka ne, don kowa sai da aka dasa masa pamponsa amma don mugunta sai ku wani kwaso shegun bokitan ku duk datti kuna kwashe min ruwa mugayen yara" Ita dai tana tsaye wannan karan ta daure fuska sai kallon ta take, A fusace inna tace "Baxa ki je ki juye min a bandaki ba ko sai nasa an kira min Bukar ya taho duk inda yake yanxu?" Daukan ruwan Budurwar tayi fuuuu ta wuce ciki, inna ta shiga parlor ta dauko wani karamin kwado ta kulle tap din ta wuce cikin parlor tana cewa "Gwara in ta tsayawa ba ruwan nima da a xo ana ta debe min a cuce ni" Tana shiga parlor ta kalli matashin dake xaune kan kujera yana danna wayarsa, ta hade rai ta dau kyallen da take goge goge ta ta fi gun kayan kallo ta ci gaba da gogenta tana cewa "Ka sake dawowa karasa sauran fitsarar da ka mance baka yi ba kenan, wato duk wanda kayi jiya bai isheka ba, to ni dai a fita a bar min parlor ba ruwana, ba katon banxan da zan kula yau ta kaina nake, kaje can kayi ma uwar ka" shi dai bai tanka ta ba sai danna wayarsa yake, Bayan wani lkci ya mike yace "Dama Abba ne yace in xo in baki hakuri" daga haka ya nufi kofa fuska daure, da karfi Inna tace "Imaan tunda mutumin nan ya shigo kinji ya ce min wani abu?? To ni dai ba ni ka ba hakuri ba wllh, idan kuma ba ka yi hankali ba sae in iya fitar har ofis in sami Ahmadu ynxu" Imaan ta rufe babban roban da ta jawo daga karkashin gado tana kokarin daure alkakin da ta cika a leda jin inna ta sake kiranta tace "Gani nan xuwa" window ta bude a hankali ta jefar da ledan ta shiga bayi ta wanke hannunta da sauri ta fito ta shiga parlor fuska daure tace "Meye kike kirana" Inna na nuna sa tace "Ke tunda kika shigo kin ji muryar bawan Allahn can?" Imaan ta tabe baki tace "Wai wa?" Inna tace "Mujaheed" Imaan tace "To ni na sani? Ni da nake cikin daki" daga haka ta bi ta gefensa ta fice a parlon, sauran kayan wankinta ta dauka ta xaga baya da sauri ta dau ledan alkakinta ta wuce part dinsu, a hankali ta bude kofar parlon tana lekan ciki ganin Ammi bata ciki ta wuce bedroom din ta da gudu ta kulle ta ajiye buckets din a bayi. Da yamma Ammi ta shigo dakin ta sameta kwance tana bacci, Ammi tace "Imaan" bude ido tayi a hankali, Ammi tace "Ki tashi daga baccin nan haka, yamma yayi, kin kwaso socks din naki da kika wanke" tana murxa ido tace "Xan kwaso" Ammi tace "Ga hijabs din ki da na wanke can clothe line din su Anty ki tafi ki kwaso su ma sun bushe, don kawai yan gidan basa nan sai ki k'i tafiya makaranta ko?" Ita dai bata ce komai ba, Ammi ta juya ta fita, xaro ido imaan tayi ta mike da sauri ta shiga bathroom din ta ta matse socks din da hula da inner wears ta xuba su a dryer na washing machine ta kunna sannan ta fita, Tana kwashe hijabs din ta a clothe line da Ammi ta ce mai gadi ya bude gate, wani rantsatsen mota ya shigo gidan direct parking space dake babban part din ya taho, sai ga wata motar ta biyo bayansa xuwa parking space din, Mutumin daxu da safe ne ya fito driver seat sanye da kananun kaya daga cikin motar farko, wata yarinya da baxata wuce Imaan ba ta fito front seat din motar, sannan wata mata da baxata haura hamsin da hudu ba ta fito back seat tare da wata yarinya mai shekara ashirin, kana ganinsu kaga yan daki daya, Imaan ta dauke kai tana ci gaba da abinda take, Bude dayar motar aka yi, wani mai kama da Mujaheed Sak ya fito sai dai shi ya fi sa haske, Shima dogo ne kuma Mujaheed ya girme sa da 4 years, mahaifiyarsa ce ta fito bayan motar da kanninsa duk mata hudu su ma, murmushi mahaifiyar tasa tayi ganin Imaan tace "A'ah wanki aka yi yan mata" Imaan tayi murmushi tana boye fuskarta tace "Sannu da dawowa Anty" Anty tace "Sannu Imaan, ya Ammi fa" Imaan tace "Tana gida" Kallon matashin da ke tsaye kusa da Anty yana kallon ta tayi tace "Ina yini ya Yusuf" yace "Lafiya lau, Imaan din daddy, sai dai nasan ba ke kika yi wankin nan ba" ta xaro ido tace "Ni nayi fa" Anty ce "Toh shi xai maki idan baki yi ba banda tsokana, share sa kin ji" tuni Mujaheed ya nufi entrance din shiga part din su mahaifiyarsa Umma dake satan kallon Imaan da ta ki kallon ta ta bi bayansa, Anty ma ta wuce Yusuf na biye da ita yana waigo Imaan yace "In ji yau baki je tsokanan inna ba ta hada ki da daddy" Imaan tayi dariya tace "Ni ina ruwana da ita ai na daina xuwa part din ta" Daga haka ta juya ta wuce bangarensu. Da daddare Imaan na kokarin saka kayan baccinta ta kwanta Ammi ta shigo dakin, tana kallon ta tace "Ki je Abba na kiran ki" xaro ido tayi tace "Abba kuma Ammi?" Juyawa Ammi tayi ta fita, kamar xata yi kuka ta saka hijab din ta ta fita tana tunanin kiran me Abba ke mata da daddaren nan. A hankali ta bude kofar parlon Abba ta shiga bayan ta cire takalmin kafarta, Abba na xaune a 3 seater cikin parlon Mujaheed na xaune shi ma kan lallausan carpet din dake malale kasa, sai Umma dake xaune kan one seater, Anty ma haka, Imaan ta karasa kanta a kasa ta xauna kasa kusa da Anty, murya can kasa ta gaida Abba, Abba ya amsa yace "Ya karatu" tace "Alhmdllh" yace "Imaan discipline din ki kenan rashin gaida na gaba da ke?" Imaan ta daga kai tana kallon sa, ya daure fuska yace "Ita Hajiya sa'ar ki ce da ba kya gaisheta a gidan nan?" Shiru tayi bata ce komai ba, ya hade rai yace "I am talking to Imaan, kuma ki bar kallona my friend" A hankali ta fara 6ata fuska tana jan yatsunta, lkci daya ta fashe da kuka, Abba ya mata tsawa yace "Daman kuka kika samu don ban xane ki ba yanxu" kuka take yi sosai kamar warce aka duka, Mujaheed ya mike ya mata wani raxanannen tsawa ta mike da gudu ta nufi kofa, xai bi ta Abba ya dakatar da shi yace "Rabu da ita M.A, Allah ya shiryeta" Umma ta tabe baki tace "yaran yanxu da ba a sangarta su ba ma ya aka kare ballantana wannan?" Anty ta mike ta fita parlon, Abba dai bai ce komai ba, imaan bata xarce ko ina ba sai sashin inna, tana shiga parlon ta xube kan kujera ta rushe da kuka, inna ta fito daki da sauri, Yusuf ma dake kwance kan 3 seater ya mike xaune da mamaki yace "Me ya faru Imaan" jikin inna na rawa tace "Me ya samu Aishar?" Imaan ta ki cewa komai sai kuka, tuni inna ta nufi kofa, cikin kuka Imaan tace "Ni ba abinda ya samu Ammina" inna ta dawo tace "Ke dai ki dinga jin tsoron Allah, da yanxu xuciyata ta buga ya kike son 'ya yana su yi, ya zaki shigo da kuka ki janyo min wata fitinar ina xaune" Cikin rawar murya tace "Ko ba Umma bace" inna tace "Wacece haka?" Imaan bata ce komai ba sai kuka, Inna tace "Warcan mata mai kama da zabiya kike nufi wai, ko ba uwarsu fitsararren yaron nan Mujaheed ba?" Imaan ta hadiye abu da kyar tace "Ita" Inna ta share wani xufa tace "Toh xata ga barbadin rashin mutunci yau kuwa, me ta maki?" A hankali Imaan tace "Shine taje ta gaya ma Abba wai ni bana gaisheta alhalin fa ko na gaisheta bata amsawa, shine Abba ya kirani...." Sai kawai ta fashe da kuka, inna tayi wani murmushi tana gyada kai tace "Biri yyi shige da mutum, Sai aka yi ya da ya kira ki" imaan ta kalleta cikin shesshekar kuka tace "Yana min fada....." Tuni Inna ta fice parlon, Imaan ta saci kallon Yusuf da yyi tagumi yana kallon ta ta mike tana turo baki ta fita. Inna na isa bangarensu Yusuf kai tsaye parlon Abba ta wuce, har sannan Abba na xaune da Umma a parlon sae Mujaheed, gaba daya daga kai suka yi suna kallon ta, inna ta tsaya tsakiyar parlon tana kallon Abba tace "Yanxu yaro tun da sauran numfashin Bukar a duniya zaka sa ma 'yar sa ido? Yanxu a kan wannan matar zaka ci mutuncin yarinyar da lafiya ma bai isheta ba sai dai godiyar Allah? Yanxu Ahmadu duk son da d'an uwanka ke maka xaka rufe ido a hadu da kai a ci mutuncin yar sa kwaya daya tal..." Kunce ha6ar xaninta tayi tana matsar kwalla tace "Naga abinda ya isheni bai ishi Allah ba..." Abba kasa cewa komai yyi da farko, can yace "Haba inna, wannan wace irin magana kike...." A fusace tace "Ohh yare nake maka da xaka tambayeni wani irin magana nake, to wllh bari ka ji, a kan Fatima a gidan nan ina iya sa6a ma ko wani mahaluki, kuma baxata gaida matar taka ba, ita katuwar gaida mutane take?" Mikewa Mujaheed yyi ya nufi kofa kamar xai tashi sama inna ta bi sa da wani shegen kallo, sannan ta ja tsaki ta maida dubanta kan Abba dake ta kallonta ta daure fuska tace "Ahmadu yaushe rabon ita matar taka ta kai kafafuwanta bangarena gaisheni? Lallai... ni a su wa xata je gaidawa? Ni din banxa xata gaidar?? To hirrrr wllh, kada wanda ya kara sa ma jikata baki a gidan nan idan ba haka ba sai in sa Bukar ya koma daya gidansa dama shi ya nace xama waje daya da kai, tunda yar sa xa a takura gwara kawai ya bar gidan...Dubi fa Mujaheed haushi ya ji yanxu don na ambaci uwarsa, kana gani saura kiris ya bangaje ni in fadi duk cikin bacin rai, to uwa ta fi uwa ne?? don me kai ma baxa ka tattala ni haka ba, duk ka bi ka daure mata kugu bata gani na da gashi a gidan nan, to mu xuba da ita xan ga ko ita ta haifo min kai duniyar, wannan ai raini ne wllh, wai taji haushi Imaan bata gaisheta ba to baxata gaidata din ba, kar ta kuskura ta sake sa min jika a baki tayi ta kanta kawai a gidan nan" shi dai Abba shiru yyi kansa a kasa, Umma ta rungume hannunta daga xaune tana kallon wani direction din, Abba ya dago yana duban mahaifiyar tasa yace "Kiyi hakuri Inna" ta maka masa wani kallo tace "Sai dai ka ba matar ka hakuri tunda na 6ata mata rai" Tana kai wa nan ta fice. Imaan har ta kusa part dinsu taga shukanta na wake da tayi a babban gwangwani a madadin assignment da aka basu a Agricultural science, a yashe duk root din ya fita daga cikin gwangwanin, ta xaro ido ta ta fi wajen da sauri, lkci daya hawaye ya kawo idonta tace "Wllh nasan Rahma ce xata kwabar min da shuka na" sai kuma ta fashe da kuka na takaici ta durkushe wajen, ba ta lura ba har Mujaheed ya iso wajen, ta juya hawaye sha6e sha6e idonta tana kallon sa ta sake rushewa da kuka, ya daure fuska yana kallon kafarta yace "Me ya faru?" Ta mike cikin rawar murya tace "Yaya kalli fa abinda Rahma tayi ma assignment dina kuma ten marks ne, xa muyi submitting ranan Friday, kalli fa har ya girma, don nawa duk yafi nasu sai ta kwabar min" ganin sai hararanta yake ta juya ta wuce tana ci gaba da kuka, fixgota yyi yana mata wani kallo yace "Shi Abban kika tafi kika yi reporting gun Inna?" Lkci daya ta tsaida kukan da take bayan ta gane biyota yyi, ta fizge hannunta ta kwasa a guje, kiris ya rage ya kamata ta shige parlonsu ta banko kofar tasa key, Ammi dake xaune parlon tana kallo ta mike tace "Meye haka Imaan?" Dariya ta fashe da ta wuce daki da sauri tace "Sauri nake in xo in kwanta fa Ammi" tana shiga bedroom din ta ta sa makulli. Har Imaan ta fara bacci wajajen karfe goma Ammi ta bude kofar dakinta, bude ido tayi Ammi ta hade rai tace "Uban me kika debo ma inna a dakinta?" Ta mike xaune da sauri tace "Na debo mata abu kuma? Haka ta ce?" Ammi tace "Kinga na raba ki da xuwa sashinta ki dauko min magana ba ki ji ko? To ki fito mata da duk ma abinda kika daukan mata gata can bakin kofa" Imaan ta turo baki ta sauko daga saman gadon ta bi bayan Ammi da ta fita, ido hudu suka yi da inna da ke tsaye bakin kofa ta tsuke fuska, Imaan ta hade rai tace "Ni me na dibar maki xaki biyo ni cikin daren nan" Inna tace "Duk cikin jikokina babu mai ta6a min kaya ban basa ba sai ke, duk kece mai mugun halin nan don haka maxa ki fito min da alkaki na, don ba a rame na bar sa ba ina sane da abinda nake ba fara haukacewa nayi ba" Ammi dai ta nemi waje ta xauna, Imaan ta 6ata fuska kamar zata yi kuka tace "Wai yaushe naje da har xan dibar maki kayan ki ni da ba ci ma nake sosai ba, to ma ba xaki gansa hannuna da xan fita ba" Wani tsawa Ammi ta yi mata tace "Kin tafi kin dauko abinda kika diba ko sai na mare ki" Imaan ta harari inna ta wuce kitchen sai ga ta ta fito da ledan alkakin, Inna ta saki baki ta warce ledan tace "Naga Ikon Allah ni Asabe, da yake Aisha ce ta xauna ta min tuyar bayan ta kwa6a dole ki kwaso ki kawo maku ku ci, to ni kar in sake ganin kafafuwanki a bangarena don halin ki abun tsoro ne, wannan ai ba tarbiya aka maki ba ki shiga har karkashin gadon mutane ki jawo kwalla ki debe min kayana, yanxu banda jinin ka jininka ne kin xata idan na ja Allah ya isa baxai bi ki ba, ni wllh darajar d'a na kike ci a gidan nan gaskiya, kar in sake ganin ki a parlona ni dai dama baki tsinanamin komai sai dai ki malale kan kujera kina mik'a, duk kin ru6ar min da kujeru" tana kai wa nan ta juya ta wuce, Imaan bata yarda ta kalli Ammi ba ta wuce daki ta rufe kofa tayi kwanciyarta tana turo baki. Maa sha Allah, I am back by Allah's grace... daily update in sha Allah, but if schl shud resume anytime soon xan dakata da posting for some weeks coz I will be having exams in sha Allah. Hope you guys will love the *book*, though I know I never disappoint my fans when it comes to writing in sha Allah....🌟⭐ *Imaan* ⭐🌟 _By Khaleesat Haiydar_✍🏻 2...... Washegari da safe Imaan ta fito parlor shirye cikin well ironed uniform dinta da beret dake kanta, kitchen ta shiga gun Ammi, Ammi dake juye ruwan shayi flask tace "Yau ma baki yi combing gashin ba koh" ta jingina da kofa cike da shagwaba tace "Wllh Ammi xafi, baxan iya ba" Ammi bata ce komai ba ta gama xuba ruwan a flask ta xuba mata nata a cup dinta ta hada mata shayin sannan ta mika mata, Karba Imaan tayi ta fita xuwa dinning, Ammi ta kai mata dankali da kwan da ta soya mata ta ajiye tana kallon agogo tace "Kiyi sauri kar su jira ki don Allah" Imaan ta xaro ido tace "Ammi kullum fa ni ke jiransu" Ammi tace "Toh kar kiyi saurin" daga haka ta wuce kitchen don yin wanke wanke, imaan na gamawa ta kai plate din da cup kitchen, ta dauko jakarta, Ammi tace "Ki duba gaban dressing mirror a daki na akwai duba daya ki dauka, dakin ta shiga ta dauko sannan ta fito tace " Ammi sai na dawo" Ammi tace "Ohk Allah ya tsare kiyi addu'a kafin ki fita, and you make sure baki mance ko wani book ba tunda hankali bai ishe ki ba" dariya kawai tayi ta fita gidan bayan tayi addu'a, Can parking space din su Yusuf ta tafi ta tsaya don nan take jiransu, yawanci Yusuf ke kai su wani lkcin kuma Anty ta ajiye su tunda tsohon driver dinsu ya tafi, Tana ta tsaye jikin mota ta hango plant din su Ummi, Rahma da Maimoon don duk ajinsu daya wato ss2, kamar xata yi kuka ta dinga kallon waken nasu da duk ya fito da ganye, ga nata can an lalata mata, kallon entrance din gidan tayi lkci daya ta nufi wajen da plant din suke da kafa ta haure gaba daya biyun banda na maimoon don kowa ya sa sunansa, sai da ta tabbatar roots din sun fita sannan ta koma jikin mota da sauri, Ummi ce ta fara fito sanye cikin uniform irin na jikin Imaan sannan Rahma sai Maimoon, Babu wanda ya kalleta cikin su banda Maimoon da tace "Imaan kin gama maths assignment din ki" Imaan tace "Ehh na gama" Maimoon tace "Toh idan mun shiga mota xan kwafa plss ban yi ba" Imaan tace "Ohk" Mujaheed ne ya fito rike da makullin mota fuska kamar hadari, Imaan ta xaro ido tana kallon Maimoon murya can kasa tace "Shi xai kai mu?" Maimoon tace "Ehh ya Yusuf baya nan ya tafi Zaria daxu, shine Anty tace ya Mujaheed ya ajiye mu, shine yake fushi" Imaan ta turo baki bata ce komai ba yana bude motar ta shiga back seat tare da Maimoon da Rahma, Ummi ta shiga gaba, har suka bar gidan babu wanda yace komai cikin su, Imaan ta bude jakarta ta ciro assignment din ta ba Maimoon, tafiyar minti ashirin ke kai su makarantar su, amma saboda gudun da yyi cikin few minutes suka iso, yyi parking dai dai makarantar yana kallonsu da kyau yace "Dama kuna tashi ku fara trekking din dawowa gida don baxan xo daukan kowa ba" a hankali Ummi tace "Ya M.A ai soon Abba xai dau mana wani driver fa" yace "Sauka malama" bude motar tayi ta fita, tuni Imaan da Maimoon ma suka fita suka shige cikin makarantar. Anty ce ta xo daukan su bayan sun tashi ranan, Anty na kallon Imaan dake ta yamutse fuska tace "Me ya faru Imaan" a hankali ta nuna mata kanta, Anty tace "Toh idan kin koma gida kin ci abinci sai ki sha magani ki kwanta ki huta" to kawai imaan tace, ko da suka isa gida har bacci ya dauketa Maimoon ta tasheta ta bude ido, Anty tace "Toh shiga gida imaan" kai kawai ta gyada mata ta fita ta nufi part dinsu tana dingishi. Ruwan xafi Ammi ta hada mata ta shiga tayi wanka sannan ta ci abinci, Ammi ta bata magani tace "Sai ki daure kiyi shirin tafiya islamiyya it's too early ki fara fashi this week, today is Monday" Imaan bata ce komai ba, Ammi na fita ta koma kan gado ta kwanta kamar xata yi kuka, hudu da minti biyar Ammi ta shigo dakin jin shiru bata fito ba, ganin har bacci ya dauketa ta kai hannu jikinta taji da dumi, girgixa kai tayi ta juya ta fita, Maimoon ne ta shigo parlorn sanye da uniform din islamiyya, Ta gaida Ammi sannan tace "Ammi imaan muke jira" Ammi tace "Bata jin dadi ku tafi Maimoon" a hankali Maimoon tace "Allah ya sauwake" sannan ta fita, Ammi na girkin dinner a kitchen wajen karfe biyar Imaan ta fito daki, wani internal heat kawai ta ke ji, kuma tana kunna Ac tasan sauran ta dinga lekan kitchen kamar xata yi kuka, a hankali ta nufi kofar fita ta bude kofar yanda baxa aji kara ba sannan ta fice xuwa part din inna don ta je ta kunna Ac, Inna na wanke gun tap dinta da take sa ma kwado ta daga kai tana kallon Imaan tace "Baki tafi islamiyyar bane yau" Imaan ta turo baki tace "Ehh" daga haka ta shige parlon, kunna Ac tayi ta kwanta kan kujera dake kallon Ac din ta lumshe ido, inna na gun tap din har sannan sai ga Mujaheed, ta mike tana kallon sa tace "Baka ji bayana ba Mujaheed kamar xai balle, ko kai baka ga yanda wajen pampon yayi haske ba tun daxu nake ta gurza gashi sai kyalli yake, ai kazanta bata da kyau, yanxu kaga ko tuwo aka xuba a wajen mutum xai iya xaunawa ya ci" Mujaheed dai bai tanka ta ba ya shige parlorn bin bayansa tayi, ya ajiye ledan hannunsa yace "Gashi Abba yace a kawo maki" tace "Toh Allah yayi masa albarka... Dama raina na son kayan marmarin" xai fita Inna tace "Mujaheed kaga yarinya nan abinda ya kawota kenan ta xo ta kunna Ac wata cutar ta kamata ace ai a parlorn inna ne, to ni dai ba ruwana ka kashe min kayana taje can ai su ma suna da shi, duk yanda aka yi kuma uwar hanata kunnawa tayi shine ta taho ta kunna nawa salon ace parlorn inna to Allah ya fi ki babu me sa ni a bakin duniya" Mujaheed ya kalli Imaan da tayi rub da ciki kan 3 seater din ya tabe baki xai fita Inna tace "kai ya ina maka magana xaka fita, idan uwar ka Rukayya ce xaka mata haka Mujaheed?" Fuska daure ya juyo ya xauna yana kallon ta da kyau yace "Wllh idan kina sa mahaifiyata a baki Hajiya xa mu kwashi yan kallo dake a gidan nan, komai sai kice uwata" Inna ta saki baki tace "Kai ni kake daga ma murya" yace "Toh ki daina sako mahaifiyata a xancen ki idan baki son a daga maki murya, ke kwata kwata rayuwarki baki son xaman lafiya daga kice wannan yayi maki sai ki ce wannan yayi maki...." Inna ta gyada kai tace "To ka tara kuma ka samu, xaka san ni ka fada ma bakar magana" Tana fadin haka ta kashe Ac dinta, Imaan ta mike xaune kamar xata yi kuka tace "Meye xa ki kashe min inna" Inna tace "Bukar yasa na kashe, na ku lalacewa yayi xaki taho min nan, ni dai a daina xuwa ana sa ni magana ana min rashin kunya gaskiya" imaan ta marairaice tace "Don Allah inna ki kunna xafi nake ji a cikin jikina" Inna tace "Toh baxa ki ji xafi a jikin ki ba ga magani nan an kawo maki tun daga Nijar kin ki amsa sai yawo kike min da hankali kamar ni xai amfana, duk tashi fadin da nake a kanki ba ki gani, mutum bai san inda xai dace ba, idan an baki magani sai kiyi biyayya ki amsa ki sha sai kiga Allah ya yaye maki wannan ciwace ciwacen da ba a san kansa ba" Imaan tace "Wa yace maki ba a san kansa ba, to ai da shi aka haifeni kuma ba warkewa...." Inna tace "Oh oh Allah, Mujaheed kaji irin fitinar da take ja ma kanta da bakinta ko, kai wannan 'ya ta Bukar anyi doluwa wllh, ke fata kike kar ki warke d'a na yayi ta cacan kudi, duk cikin jikokina babu mara tunani dama irin ki" Imaan ta hade rai tace "Ehh na ji, ki kyaleni da ciwo na Babu ruwanki, baxan kuma sha maganin ba don ina da na asibiti da nake sha, ni bance ki dinga amso min magani ba dama ai" inna tace "Kada Allah ya sa ki sha, to ni Allah na tuba a haka ma wa xai yi sha'awar aurem ki yau ciwo gobe lafiya duk tattalin arxikinsa ya kare a asibiti, tun kina mitsitsiyar ki nake wahala da ke kan maganan magani shi sa ma kika yi kyan gani, ke da kike kamar kwarangwal da taimakon Allah da taimkona da magungunan da nake amsar maki gun malamai shine kika marmaro, in dan ta uwar nan taki ce ai sai dai ki mutu tana kunshe daki ba fita xata yi ta nemo maki magani ba tana jiran na asibiti, Toh wllh daga yau na fita harkan ku ki ji da ciwon ki nima inyi ta kai na" Imaan ta fashe da kuka tace "Ehh naji, ki kyaleni tunda ba dole bane shan maganin ki" daga haka ta fice daga parlorn da gudu, Inna tace "Duk xa ku yi bayani bari iyayen naku su dawo" Mujaheed ya tabe baki ya mike ya fice mata a parlorn shi ma. Imaan na kwance kan kujera bayan isha Ummi ta bude kofar parlorn tana tsaye daga bakin kofa tace "Abba na kiran ki a bangaren Inna Imaan" daga haka ta fita, Ammi dake cin abinci xaune parlorn ta kalli Imaan da ta wani juya bata dai ce komai ba, bayan kusan minti biyar Ammi tace "Amma dai kin ji abinda tace Imaan" Ta juyo kamar xata yi kuka tace "Wllh Ammi kafana ciwo yake min ban san ko xan iya tashi ba" Ammi ta galla mata wani harara tace "Sai ki rarrafa ai tunda baxa ki iya tashi ba" hawaye cike idonta ta mike ta sa Hijab ta fita tana taka kafar da kyar. A hankali ta bude kofar parlorn Inna ta shiga da sallama, Abba ne xaune parlorn sai Inna da Anty, Imaan ta sunkuyar da kanta ta karasa kusa da Anty ta xauna kanta a kasa ta gaida su, Abba da Anty kadai suka amsa, inna ta wani tsuke fuska, Imaan dai bata ko kalleta ba, Inna tace "Wato shi Mujaheed din jira yake kaje ka ciccibo sa da kanka koh?" Abba ya kalli Imaan yace "Tashi ki tafi can bangaren ki kira min Yayanku" Imaan ta mike ta d'an harari inna ta gefen ido ta fice a parlorn, tana isa part din su Mujaheed ganin bbu kowa parlor sama ta haura ta tsaya corridor tana kallon door din dakinsa har ta mance rabon da ta je kusa da kofar, bude kofar Umma aka yi sai ga shi ya fito, ta matsa da sauri don kusa da kofar dama take tsaye tace "Abba yace in kira ka" ko kallon ta bai yi ba ya fara sauka stairs, ta murguda masa baki ta bi bayansa, har suka isa part din Inna bai juya ba, ya bude kofar ya shiga da sallama, kusa da Anty Mujaheed ya durkusa kansa a kasa, Abba sai kallon sa yake yana girgixa kafa, Imaan ta shigo parlorn ganin inda ya durkusa tace "Waje na ne nan" Murmushi Anty tayi, shi kam ko kallon ta bai yi ba balle ya motsa, Inna tace "Ahmadu na fa gaji da xama nan kamar warce xa a ma gafara, aji da ni in tashi in shiga ciki in kwanta" Abba ya kalli imaan yace "Samu wani wajen my friend" ta harari Mujaheed ta koma wani wajen ta xauna, Abba na kallon Mujaheed yace "Muhammad ita innar ka mayar abar wasar ka a gidan nan?" Inna ta tabe baki tana jijjiga kafa, Mujaheed bai dago ba kuma bai ce komai ba, Abba yace "Am I not talking to Mujaheed" ya dago a hankali yace "Abba kayi hakuri don Allah" Abba yace "Stupid, ni ma kake ba hakuri?" Ya kalli inna yace "Kiyi hakuri inna" dakatar da shi tace "A'a malam a gaban ubanka xaka ce min inna kenan, wllh Ahmadu daxu yana nuna ni da yatsa a can bakin kofar kamar xai make ni Hajiya yace min, ni na ma xata duka xai kai min bayan ya gama kashedin, to gaskiya da sake, sam yaranka basu da d'a'a basu da kunya Ahmadu, isuhu ne kadai dama mai gudun bacin raina duk da shi ma ko aiki xai kashe ni baya taimakona, to ynxu Mujaheed da wani ne da ya xo ya gan ni durkushe ina faman gurje gun pampo ba amsa xai yi ba ya taya ni, to wllh bai amsa ba sai xagina ma ni da yayi daga karshe, a xo har sashina a dinga ci min mutunci, to hirrr don duk ranan da aka isheni tattara kayana xan yi in bar gidan nan kuma sai anyi shekara duba ana nemana" Mujaheed ya d'an daga kai ya kalleta ta gefen ido ya maida kansa kasa, Abba dai bai iya yace komai ba, Anty tace "Kiyi hakuri inna, a yafe masu" Inna tayi kasa da murya tace "Wllh Amina daga nace kai kuwa Mujaheed haka kake ma Mamarka a gida ina ma magana xaka wuce, kuma fa cikin lallami nayi tambayar kawai ba sai ya sakar min aradu a kai ba, ita kuma wancan lankwasasshiyar mai kama da yar tsana bbu abinda ta mance bata gaya min ba daga nace Imaan ga maganin da na amso maki saboda ciwon ki da ba a san kansa ba ba a san dalilinsa ba, wllh Ahmadu sae kaga wanke ni da yarinyar tayi tasss har da ce min ba ruwana da ciwonta kuma ciwon ba me warkewa bane" Imaan ta fashe da kuka har da shessheka, Abba yyi mata tsawa cikin rawar murya tace "Abba xagina fa ta ke yi wai...." Abba ya dakatar da ita yace "Keep shut" ta hadiye abinda xata ce tana hawaye, Mujaheed yace "Kiyi hakuri Inna" Inna tace "Atoh ya xan yi idan ban hakura ba, dama wanda aka cuta ake ba hakuri, amma daga kai har ita kar in sake ganin kafufuwanku a bangarena, tunda kun raina ni, Isuhu da Maimuna sun ishe ni" Fada sosai Abba ya dinga ma Mujaheed da kansa ke kasa, inna sai matsar kwalla take ita a dole an 6ata mata rai, hakuri Mujaheed ya kara bata, Anty ta sa Imaan ma ta bata hakuri, mikewa Imaan tayi da sauri ta fice parlorn tana kuka, Inna tace "Sai ubansa na magana yayi ta sinne kai kamar na kirki alhalin crooo kenan ku ke gani, kar ka sake xuwa min sashi ni dai na gama magana" Mujaheed bai kalleta ba balle ya tanka ta ya mike ya fice parlorn, can kusa da wani flower ya ga Imaan durkushe tana kuka, ya dinga hararanta har ya isa wajen da take, ta mike cikin rawar murya tace "Yaya don Allah kai kaji na xage ta daxu?" Ba tare da ya tsaya ba yana ci gaba da tafiya yace "Ke ma ai ba dukan ki naga aka yi ba" Ta bi shi da kallo tana shessheka.🌟⭐ *Imaan*⭐🌟 _By Khaleesat Haiydar_✍🏻 3...... Imaan ce xaune kitchen sai faman xuba surutu take ma Ammi dake girkin dinner a kitchen, yar skirt ne jikinta sai ves da yake ranan alhamis ne babu islamiyya, Ammi dake ta saurarenta ta tabe baki daga karshe tace "Aikin kenan sai dai ki cika mutum da surutu ba taimakon fari balle na bak'i" shiru Imaan tayi tana kallon Ammi, Ammi ta kalleta ganin yanda mood dinta ya canxa tayi murmushi tace "Toh ci gaba ina jin ki" sunkuyar da kanta tayi bata ce komai ba, Ammi ta karasa kusa da ita tace "I was joking sweetheart, tafi ciki let me fry some onion and pepper" mikewa Imaan tayi a hankali xata wuce Ammi ta bi ta da kallo har ta fita, Ammi ta jingina da cabinet din kitchen din ta sauke ajiyar xuciya, can ta nufi kofa ta fita don bata son tayi bacci coz shine next abinda xata yi in har ta shiga daki, dakinta Ammi ta shiga ta sameta har ta kwanta, Ammi tace "Baxa kiyi bacci ba yanxu yamma yayi, je dakina xa ki ga leda da atamfa a ciki kan dressing chair ki kai ma su Anty kice ankon bikin Halima" Imaan ta mike xaune tace "Ammi to na mu fa" Ammi tace "Sai ki kirata ki tambayeta ban san ko an fidda naku ba" Imaan tace "Toh, Anty kawai xan nuna ma?" Ammi tace "Ehh sai ki ce mata ta nuna ma Hajiya, na dai fita ai" daga haka Ammi ta fita dakin, imaan ta sa hijab har kasa kan kayana jikinta ta fita ta dau ledan ankon a dakin Ammi, tun da ta shiga parlonsu Anty take yamutse fuska ta dalilin yaji dake tashi sosai daga kitchen, lkci daya ta rike numfashinta, har xata juya ta fita sai ta nufi stairs da gudu don ta shiga dakin Anty, tsarkewa tayi sbda rike numfashin da tayi ga kuma gudun da take, lkci daya ta fara tari sosai breathing dinta na sama, dai dai corridor ta fadi tana kokarin jan numfashi, Maimoon ta fito dakin Anty ganinta ta durkusa gabanta da sauri tace "Subhanallahi me ya faru Imaan" sound din faduwarta yasa Mujaheed ya fito daga bedroom din sa, ganinta a kasa ya kalli kofar Ummarsa kafin ya karasa da sauri ya dagata yana kallon Maimoon da ta rikice yace "Tafi ki karbo inhaler dinta da sauri" da gudu ta sauka xuwa part din su Imaan, Mujaheed ya bude kofar dakin Anty ya shigar da ita ya xaunar da ita kasa ya jinginar da ita da gado ya cire Hijab din jikinta, dai dai nan Anty ta fito daga bandaki, a rude tace "Subhanallahi, Asthman ne, garin Yaya? Ko in amso inhaler dinta" yace "Maimoon taje amsowa" sosai imaan xata baka tausayi saboda ynda take struggling da numfashinta, Mujaheed ya mike ya fita don bin bayan Maimoon suka kusa cin karo bakin kofa, fixge inhaler din yyi ya juya ya koma dakin ya durkusa gabanta ya kai mata baki, dafe hannunsa tayi tana inhaling, Anty dai na tsaye sai kallonta take cike da tausayinta, bayan wani lkci numfashin nata ya fara fita a hankali yana kokarin dawowa normal, Anty ta xauna gefen gado tayi tagumi tana kallonta, Ummi da Rahma na tsaye bakin kofar suna kallonta su ma, Har sannan Mujaheed na duke gabanta idonsa a kanta, muryar Umma suka ji tana cewa "Lafiya me ya faru ku ka tsaya cirko cirko bakin kofa?" Rahma tace "Asthma ne ya tashi wai" Umma ta leko dakin ganin Mujaheed ta wani xaro ido tace "Me Mujaheed yake a nan?" Mikewa yyi da sauri, ta wani hade rai tace "Tambayar ka nake, me ka shigo yi, ko kayi kama da likitan ta ne?" Ya girgixa kai yace "No na xo wucewa ne...." Dakatar da shi tayi tana masa wani shegen kallo tace "Sai ka tsaya aikin da ba lada koh? To ka shiga hankalin ka, Ka guji bacin raina, basu da number likitan ta ne ko kuma neman suna kake?" Shiru yyi bai ce komai ba, Cikin tsawa tace "Xo ka fita malam bana son shishshigi da kwala kai a faranti, kanwar uwar ka ko ta ubanka?" Bai ce komai ba ya kalli Imaan da Anty ke kokarin kwantarwa kan gado ya juya ya nufi kofa xai fita, Anty ta tabe baki tace "Ciwo dai bai wuce kan kowa ba, ita ma ba ita ta doro ma kanta ba....." Umma ta katse ta da sauri tace "Allah yayi mana tsari da irin wannan ciwo nata, ya tsari jikokinmu da tatta6a kunne, a rayuwar nan ta ynxu wa enda ba sickler ba ma ya suka kare, ae irinsu ne ke tsiyata namiji a sintirin asibiti...." Tsaye Mujaheed yyi bakin kofa yana kallon Umma, Anty ta wani hade rai tace "Kinga ki daina kiranta da sickler ita din ba sickler bace, Allah kuma yyi mata tsari da shi" Umma ta wani tabe baki hade da dariya tace "Kwa dinga boye ma wanda ku ka raina ma wayo, Allah dai ya ba kowa lafiya...." A hankali Mujaheed yace "Umma ba fa sickler bace, she is just a carrier...." Umma ta maka masa wani kallo tace "Meye maraban dambe da fada? And did you have any problem with her being a sickler or not da har kake karyata ni Mujaheed?" Bude kofar yayi ya fita dakin bai ce komai ba, ta ja tsaki ta fice ita ma. Anty ta girgixa kai ta zauna kusa da Imaan da ta lumshe ido numfashinta na sauka a hankali tana mata sannu, sai da ta ga alamar tayi bacci sannan ta mike ta fita, Imaan bata dau lkci tana bacci ba ta tashi ta dalilin ciwo da kirjinta ke mata, ta dinga juye juye kan gadon hawaye na xuba idonta, bude kofar dakin aka yi Mujaheed ya shigo, ya karasa kan gadon yana kallonta, daure fuska yyi yace "Me ya faru kuma?" Kirjinta ta nuna masa ta fashe da kuka, yace "Toh kukan ne xai sa ya daina ciwo, tashi xaune" mikewa tayi ta xauna da kyar, sai ga Anty ta shigo dakin, da sauri ta isa gadon tace "Me kuma ya faru Imaan, are you feeling pain anywhere?" Ta gyada kai tana nuna kirjinta, Anty ta dau Hijab ta nufi kofa tana cewa "Bari in je in kwaso magungunanta dai" Xaunawa Mujaheed yyi gefen gadon, ta koma xata kwanta yace "Kar ki kwanta" ta jingina da gadon tana goge idonta, ba a dau lkci ba Anty ta dawo da ledan maganin gaba daya, Mujaheed ya amsa yana duba maganin ya cire mata wanda xata sha, still yyi jin an bude dakin Umma, sai kuma ya ji muryarta tana tambayar inda yake, tashi yyi da sauri ya tafi bayan kofa ya tsaya, Anty ta tabe baki ta balli maganin ta dau table water ta mika ma Imaan, bude dakin aka yi Umma ta kare ma dakin kallo kafin ta tabe baki ta kulle, Shi dai yana tsaye bayan kofar, Anty ta sa Imaan ta kwanta bayan ta sha maganin sannan ta kallesa tace "Don Allah ka fita min a daki malam, tunda aikin xumuncin ma ba so ake kayi ba, kai ma kuma tsoron yi kake, yau ko da ace baka san Imaan ba a matsayin ka na likita ka ganta a wannan hali ai baxa ka ki taimaka mata ba balle tana yar uwarka halak malak, Allah dai ya shiryi mahaifiyar ka" shi dai bai ce komai ba, bayan karin mintuna uku ya bude dakin ya fita. Anty na xaune kan darduma bayan ta idar da magrib Imaan ta tashi daga baccin da ya kara dauketa, Anty tace "Sannu ya jikin Imaan" a hankali tace "Na ji sauki" Anty tace "Toh shiga bayi kiyi alwala ki xo kiyi sllh" ba musu ta mike ta shiga bandakin ta dauro alwala ta fito Anty ta mike kan darduman ta fita, Imaan ta sa Hijab dinta ta hau kai ta tada sllh, tana ta xaune kan darduman bayan ta idar sai ga Anty ta shigo da plate din abinci dakin. Imaan na gama ci ta mike rike da plate din tace "Anty sae da safe" Anty tace "Au baxa ki kwana nan ba" murmushi tayi ta make kafada ta nufi kofa, Anty tace "Toh baki fada min ko na meye atamfar ba" Ta juyo da sauri tace "Lahh, Ammi ce tace in kawo maku ankon bikin Anty Halima" Anty tace "Ashe abu ya xo dai, toh ki ce mata xan shigo gobe" Imaan tace "Toh" Anty tace "Allah ya sauwake Imaan" murmushi tayi a hankali tace "Ameen" daga haka ta fita, tun da ta sakko downstairs umma ke mata kallon tsana tana tabe baki, Imaan dai bata ko kalleta ba ta nufi kitchen rike da plate din, Rahma ce kitchen din ta gama wanke wanke, sai Mujaheed dake tsaye yana xuba ruwan Lipton daga teapot a cikin mug, Imaan xata ajiye plate din, Rahma tace "Kinga plate mai datti a wajen ne malama" turo baki tayi ta dau morning fresh ta bude xata wanke plate din, Rahma tace "Ya M.A in debar maka abincin ne xan fita?" Ya harareta yace "Abincin da ku ka cika yaji ko wanda ba yaji?" Yar dariya tayi tace "Ya Mujaheed yajin fa ba yawa" tsaki yyi yace "Ance maki ban yi tasting abincin bne ku dinga cika ma mutane ya ji a abinci kamar mayyu" Tace "Toh in maka cous cous?" Yace "I will take tea" Imaan ta gama wanke plate din ta juya ta fita kitchen din. Kallonta Ammi ta dinga yi bayan ta shigo tace "Ya jikin Imaan" tayi murmushi tace "Na ji sauki Ammi" daga haka ta nufi dakinta Ammi ta bi ta da kallo. Karfe sha daya saura Ammi ta shiga dakin Imaan, ganin tayi bacci ta tasheta tana mika mata wayar hannunta tace "Me ya sa kika kashe wayar ki" Imaan na murxa ido tace "Kila mutuwa yyi ba charge" Ammi tace "Toh idan kin gama ki maido min wayata daki" Imaan tace "Toh" sannan ta kai wayar kunne tace "Daddy ina yini" Daga daya bangaren ya amsa yace "Why is ur phone switched off" ta langwabar da kai tace "Daddy ban sa a charge ba tun jiya" yace "Toh kiyi kokari ki sa ya jikin?" Tace "Naji sauki, daddy ina missing dinka yaushe xaka dawo?" Yace "Weekend in sha Allah" ta wara ido cike da jin ddi tace "Plss daddy ka dawo week end din kar ka daga, wllh ina son in ganka" kamar xata yi kuka ta kare, yyi murmushi yace "Sure dear, plss ki daina wasa da shan drugs din ki kinji" tace "Ina sha Allah daddy, har yanxu Dr ma bai xo ba" yace "Ehh mun yi waya daxu yace bai dawo ba" Imaan tace "Toh" yace "Sleep tight dear, banda kunna Ac" yar dariya tayi tace "Toh daddy byeee" katse wayar tayi ta mike ta kai ma Ammi daki sannan ta dawo dakinta ta shige duvet. Yau Friday Imaan na dawowa schl bayan tayi wanka tana kokarin saka kayanta taji k'aurin abincin da Ammi ta bar mata a kitchen kan gas don tana shigowa gidan Ammi ta fita kasuwa yin cefane, da gudu ta fita daure da towel don kashe gas din don dama sae da Ammi tayi mata kashedi kan cewar kada ta yarda abincin ta ya kone, muryar inna ta ji a balcony tana cewa "Aa kawai ni dai naga kwana biyu bata shigo bane shine nace in xo in duba ko jikin ne, tunda haka Allah yyi ta mai laulayi, ni jiya ma ko abinci basu kawo min ba wllh, in ma ba ta da lafiya ita Aishar baxata iya takowa ta kawo min abincin ba tunda ba uwarta Habiba bace, abu dai gashi ba tsari da ni fitinanniyar tsohuwa ce ba Bukar xan kira ince matarsa ta bar ni da yunwa ba?" muryar Yusuf imaan taji yana dariya yace "Toh ae an kai maki daga gidanmu naga" da sauri Imaan ta shige daki ta dau Hijab dinta ta fito ta shige kitchen ta kashe gas din sannan ta bude kofar kitchen din ta fice tana murguda baki ta sa Hijab dinta da iyakarsa gwiwa, ko takalmi bbu kafarta ta dinga tafiya har ta zagayo front din gidan, Mujaheed ne xaune kan farin kujera yana waya, ta turo baki ta wuce sa da sauri, ko minti biyar ba ayi da wucewarta ba shi ma ya ji muryar inna tana tahowa, mikewa yyi da sauri tun kan ya bar wajen ta gansa, da karfi ta kwalo masa kira tana murmushi, ya ki juyowa har ya sha corner, Yusuf sai danne dariyarsa yake, Inna ta bude baki tace "Wato ni Mujaheed xai walakanta ina kiransa ya min banxa kai shaida ne ko Isuhu" tana magana tana kunce ha6ar xanin xata goge kwalla, Yusuf ya kasa daurewa ya fara dariya yace "Ke fa kika ce kar ya sake xuwa bangaren ki..." A fusace tace "To shi mahaukaci ne bai san bacin rai ba" Karo Mujaheed ya kusa yi da Imaan dake kokarin lekowa taga ko inna ta taho bangaren, ya hade rai yace "Baki gani ne?" Tana shafa Inda ya bugeta tace "Ko ba inna bace, ta wani biyoni gidanmu anjima tace ina mata rashin kunya" tafiyarsa yyi ya bar ta wajen tsaye, ta turo baki ta bi bayansa, jin tafiyarta a bayansa ya tsaya ya juyo yace "Wai me yasa kike bi na ne" Tace "Ni ba bin ka nake ba tafiyata kawai nake" Tsayawa yyi ya daure fuska yace "To yi tafiyar ki, bana son ganin ki kusa da ni" ba ta ce komai ba ta fara tafiya kamar mai counting steps dinta, yana ta tsaye yana jiran tayi nisa ganin ynda take tafiyar ya girgixa kai ya wuce ta cikin lokaci kankani, sai a sannan ta kara saurinta har ta jera da shi, d'an murmushi yyi bai dai ce komai ba bai kuma kalleta ba, sai da suka kusa entrance din kitchen din part dinsu tace "Yaya ka mance promise da ka taba min 2 years back koh?" Kallonta yayi kamar baxai ce komai ba sai kuma yace "Na me?" Ta wara manyan idanuwanta tace "Idan nayi saukan al-quran, gashi mun kusa in few months time" tabe baki yyi xai bude kofar kitchen din yace "I can't recall...." Ta xaro ido ta rikosa da sauri tace "Wllh nasan baka mance ba" Buge hannunta yyi yana mata wani kallo yace "Keee" Ta turo baki tana kallonsa, yace "Sakeni kar in mare ki" sake sa tayi ya bude kofar kitchen din ya shiga ya kulle, tana ta tsaye wajen bayan few minutes ta murguda baki ta wuce, ta kitchen dinsu ta bi ta kulle kofar sannan ta wuce dakinta ta sa kayanta. Yau tunda Imaan ta tashi take ta murna, gaba daya farin cikin ta ya kasa boyuwa, Kitchen ta shiga tace "Ammi da yaushe daddy xai iso?" Bude baki Ammi tayi tace "Kina kallon agogo kuwa Imaan?" Imaan tace "Ammi wai yau ma da daddyna xai dawo sai naje islamiyya?" Ammi ta mata wani mugun kallo tace "Uwar me xa ki xauna ki min ko yace maki da safe xai taso, common kin 6ace min a nan kin je kin shirya ko sai na 6ata maki rai" a hankali Imaan ta juya a sanyaye ta koma bedroom dinta ta fiddo uniform dinta ta shiga sa wa, sai da Ammi tayi mata jan ido ta amince da yin breakfast da ta hada mata, tana xaune dinning tana shan shayin da kyar Maimoon ta shigo parlon sanye da uniform, Ammi dake goge goge a parlorn tace "Maimoon ku yi wucewar ku kar ta bata maku lkci ko da kafa ne sai ta je" dariya kawai Maimoon tayi ta fita, Imaan ta mike don kanta ganin takwas ya wuce ta dau jakarta ta fita tana matsar kwalla ko ta kan kudin makarantar bata bi, Ammi dai ko kallonta bata yi ba, Tsaye taga Mujaheed jikin motar banda masifa babu abinda yake ma kannin nasa, duk kallonsa kawai suke babu wanda yace komai, "Don samun waje nan nan da islamiyyar ma sai an kai ku a mota ku ga yan gayu ko, to wllh ni ba driver din kowa bane a cikin ku da xa a dinga cewa in ajiye ku a makaranta, Yusuf da ya ga xai iya sai yyi, I won't tolerate that shittt" A hankali Ummi tace "Amma ya Mujaheed kawai don kana nan ne yasa xaka kai mu ai ba kai ke kai mu ba dama, kuma Abba yace kila Monday xa mu samu sabon driver...." wani kallo ya dinga mata fuska daure, ta sunkuyar da kanta, Imaan da isowanta kenan ta bude motar xata shiga ya dakatar da ita yace "Kee, do I look like drivern gidanku da xaki ajiye ni for the past 15 mins a nan, to ke daga yanxu ma xa ki fara naki trekking din" yana fadin haka ya nuna mata makeken gate din gidan yace "Bi can ki kama hanyar makarantar" ta wani gwalo ido tana kallonsa, lkci daya ta juya kamar xata yi kuka xata koma part dinsu tace "Ni dai ban ta6a tafiya da kafa ba...." Wani tsawa yyi mata yace "Wllh ki ka yarda na takowa har Inda kike sai na sa ki kuka" tsayawa tayi tana hawaye don bata mance last abinda ya mata ba, ya nuna mata gate on a serious note yace "Bi can" Gate din ta nufa tana kuka ya jira ya ga fitar ta sannan ya shiga motar ya bar gidan har ya wuce ta. Tsaye tayi bakin titi ta rufe fuskarta da Hijab tana kuka, ta kusa minti sha biyar tsaye a haka taji cikin cool voice ance "Are you okay" xame hannunta tayi a hankali daga fuskarta tana lekan ko waye ta cikin hijab dinta, wani dogon matashi ne da baxai wuce thirty two ba, yana sanye cikin kananun kaya idonsa sanye da bakar spec, dogo ne shi din sosai, sannan shi ba baki ba kuma baxa a sa shi a jerin farare ba, kuka ya kara taho mata ta dinga rerawa, yace "Subhanallah, wani abu ya faru da ke ne? Talk to me plss" Cikin rawar murya tace "Yaya ne ya ce baxan shiga mota ba trekking xanyi kuma islamiyyar mu da nisa wllh" kallonta ya dinga yi da mamaki, ta sake lekosa ta cikin Hijab suka hada ido ta yi saurin rufe fuskar tana shessheka, ya d'an yi murmushi yace "Kin masa laifi kenan" girgixa masa kai tayi, yace "Toh mu je in ajiye ki ga ride dina can, while going inside the filling station na gan ki tsaye bayan nayi refilling tank na fito I still saw u the way you were so I decided to check if you are alright" shiru tayi bata ce komai ba yace "Mu je to" tace "A'a" yace "Ohk in samar maki adai daita?" Kai ta gyada masa, ya tsayar da adai daitan ta shiga ya basa kudin, a hankali tace "Nagode" ya mata murmushi kawai mai adai daitan ya ja suka bar wajen, Yusuf ne ya dauko su daga islamiyyar bayan sun tashi karfe sha biyu, tun a mota ya dinga tambayar Imaan me ya faru ganin yanda take yamutse fuska, da kyar tace "Kafana ke min ciwo" yace "Toh sannu, idan muka isa gida sai ki shafa maganin" a hankali tace "Toh" suna isa gidan da kyar ta fito motar, Yusuf ya kama hannunta ya rakata har sashin nasu sannan ya bude mata kofa ta shiga ciki, wanka kawai tayi ta saka doguwar riga Ammi ta shafa mata methylated lotion din da take shafawa a kafafuwanta sannan ta sa ta kwanta nan da nan kuma bacci ya dauketa, dab da la'asar Ammi ta tasheta, Ammi bata mata xancen islamiyya ba Imaan ta wara ido ganin irin girke girken da Ammi tayi tace "Ammi is all this for daddy?" Ammi tace "No it's for Imaan" murmushi Imaan tayi ta rungumeta ta baya tace "Thanks sweet mum" Ammi tace "Ki tafi kiyi sllh ko baki ga lokacin hr ya gota ba" da sauri ta koma daki, tana idar wa ta fito, Ammi tace "Daddy ya kira yana gate, ki fita ki shigo masa da kaya" da sauri Imaan ta nufi kofa Ammi na kiranta ta xo ta sa hajib don rigar jikinta karamin hannun garesa amma tuni ta fice, dai dai nan mai gadi ya bude gate sai ga motar Daddynta, da gudu ta nufi parking space ta tsaya cike da murna, Mujaheed dake kokarin bude motarsa suka yi ido hudu da daddy da ya fito Imaan ta rungumesa, Daddy ya sakar masa murmushi, hakan yasa ya nufe sa kamar mai kirgan steps dinsa, daddy na shafa kan Imaan yace "Ba kya girma koh Mamata" ta kara kankamesa tace "Don Allah daddy ka daina dadewa haka wllh ina Missing dinka" yyi murmushi yace "To xan daina mamana" Mujaheed ya risina yace "Sannu da hanya Abba" Wani hade rai Imaan tayi tana hararansa ta gefen ido, Daddy na murmushi yace "Thanks Son, ka bar mu a birnin tarayya ynxu koh" murmushi Mujaheed yyi yace "Ae kam daddy" daddy yace "Toh Allah yayi jagora, ya aikin fa?" Yace "Ae ban fara ba sai Monday Abba" Daddy yace "Allah ya kai mu" Daddy ya mika ma Imaan da ta turo baki ledan apples dinta da chocolates don a ko da yaushe tsaraban ta kenan, Mujaheed dai ko kallonta bai yi ba ya dau jakar laptop din daddy da wasu files ya nufi part dinsu, Murguda baki Imaan tayi ta jera da daddynta tana ci gaba da gaya masa yanda tayi kewarsa, Mujaheed ya sunkuyar da kai ya gaida Ammi bayan ya ajiye jakar hannunsa da files, ta amsa ta dau jakar ta wuce daki, Daddy ya xauna yace "Barrister bai dawo ba ko Mujaheed?" Mujaheed yace "Ehh bai dawo ba" Daddy yace "Ohk mun yi magana daxu ma" Mujaheed ya dukar da kai yace "Toh Allah ya huta gajiya Abba" daddy yace "Madalla nagode son" har ya fara tafiya Daddy ya kalli ledan apples da chocolates da Imaan ta sa gaba tana dubawa yace "Son baxa ka Debi apples ba" Da sauri Imaan ta jawo ledan jikinta tana kallon daddy, Mujaheed da har xai ce A'a don he isn't a fan of Apple ganin abinda tayi yayi kasa da kai yana shafa gashinsa yace "Toh Abba" daga haka ya nufeta, bude baki tayi tana kallon daddy lkci daya hawaye ya kawo fararen idonta, Mujaheed ya jawo ledan yana kallonta da kyau ya cire spare leda ya debi apples har hudu a cikin guda takwas da Daddy ya siya ya xuba a wani ledan yana kallonta har sannan, ya kara bude ledan chocolates din ma ya debi mai yawa ya xuba a ledan hannunsa, har ya mike ya sake dawowa ya dau Apple daya ya sa ka a ledan, daddy ya dauke kai yana murmushi, Mujaheed bai yarda ya kallesa ba yace "Nagode Abba" daga haka ya fice parlon.🌟⭐ *Imaan*⭐🌟 _By Khaleesat Haiydar_✍🏻 4..... Daddy ya kalli Imaan dake goge hawayen idonta yace "Don yayanki ya debi apples kike kuka Imaan?" Ta marairaice tace "Toh daddy ai ba shi ka siyo ma ba gashi ya kwashe min gaba daya kuma wllh baya cin apple" Daddy yyi murmushi yace "Shi yace maki bai ci" cikin rawar murya tace "Ae nasan baya ci tun da can" Daddy yace "Toh anjima idan na fita xan karo maki" a hankali tace "Toh nagode" yace "Wai amma me ya hada ku da yayan naki all of a sudden Imaan" Ammi da ta fito parlon tace "I am still wondering also, lkci daya aka yi parting" Daddy yace "Ko kin masa wani abun ne dai" ta turo baki ta dawo kusa da daddy tace "Kawai dai naga ya xama mugu ne shi sa na daina kulasa" Dariya kawai daddy yayi, Ammi tace "Har nan ma ai baya shigowa yanxu" Daddy yace "Toh Allah ya kyauta" Imaan tace "Daddy ni dai ka daukan min personal driver dina plss" daddy yace "Ba Abbanku xai daukar maku driver ba, ai mun yi magana da shi bayan tsohon drivern ya wuce" Tace "A'a daddy ni dai nawa daban nake so, kilan ba yanxu driver din ma xai xo ba, yau fa Yaya bai bari na shiga motar ba don na bata masu lkci da kafata na tafi islamiyya shi sa tun da na dawo duk jikina ke ciwo sai da Ammi ta shafa min magani na kwanta da na tashi shine naji sauki"' Murmushi kawai Daddy yayi ya mike yace " Bari in yi wanka daughter " daga haka ya wuce bedroom dinsa, Ammi tace "Sai ki tashi ki kai ma Inna abinci ko yau ma baxa ki ba" Ta kalli Ammi da sauri tace "Ammi ca tayi bata son sake ganin kafata a part dinta fa, kuma in je yanxu ta gaya ma daddy" Ammi tace "Tashi ki dauki abinci ki kai mata nace" Daga haka Ammi ta bar parlon, mikewa Imaan tayi ba don ta so ba ta shiga kitchen, kusan duk abinda Ammi tayi ma daddy sai da ta dibar ma inna duk ta ajiye a basket, Imaan ta dau basket din me dauke da abincin ta fita, har ta isa part din Inna fuskarta a daure yake irin ko kulata din nan baxata yi ba, ta dinga kallon takalman dake bakin kofa kafin ta bude kofar ta shiga, Mujaheed na xaune yana kallon inna dake bada labari tayi mitsi mitsi da ido, banda murmushi babu abinda yake don da wuya yake dariya, su Maimoon da Rahma kuwa dariya har da kyakyatawa, Inna ta saita hannu sama tace "Ji kawai muka yi ratatatata.... Ba sai kakan ku ya shige karkashin gado ya bar ni da halina da 'ya yana ba, lkcn Bukar na bayana sai tsala ihu yake, Ahmadu kuwa fitsari ya dinga saki yayi sau uku a wando...." Ganin Imaan Inna tayi shiru ta jawo daya daga apples biyar dake cikin leda a gabanta ta kai baki, Har sannan su Maimoon dariya kawai suke, imaan ta ajiye basket din hannunta tana kallo chocolates din da Daddy ya kawo mata a hannunsu Maimoon, ta saci kallon Mujaheed ta juya xata fita Inna ta tabe baki tace "Ga dambun naman ki can a daki ni dai na ajiye maki bana bi ta halin ki ba" ba tare da ta juyo ba tace "Bana ci" inna na ci gaba da cin apple dinta tace "To wa yayi asara?" Mujaheed yace "Yana ina a dakin?" Da sauri Imaan ta juyo ta shige dakin, Inna tace "Ya xaka ce yana ina bayan ka ci rabon ka da wanda ma ka dauka ban baka ba" yace "Haba" tayi tsaki tace "Yana nan cikin roba xa ki gansa a rufe, duk naki ma ya fi yawa" Imaan ta fito rike da uban dambun naman da inna ta ajiye mata a bowl mai murfi ta nufi kofa, inna tace "Wannan liyafar hala Bukar ne ya dawo?" Imaan tace "Bai dawo ba" daga haka ta fita, Inna tace "Duk ta ma fige kamar bata cin abinci" Rahma tace "Mu dai ci gaba da ba mu labarin da kike yi don Allah inna" inna ta gyara xama xata ci gaba, mikewa Mujaheed yyi ya fita parlon. Imaan na komawa bangarensu ta tadda Yusuf ya shigo gaida Daddy, Ya bi ta da kallo ta boye bowl din hannunta tana wara masa manyan idanuwanta tace "Nasan ka ci naka dai" fitowar Daddy parlon yasa Yusuf bai ce mata komai ba, daddy yace "Engnr ashe kana gari" Yayi murmushi yace "Ina nan daddy, da fatan kun iso lafiya" yace "Alhmdllh My son, ya aikin fa" Yace "Mun gode Allah Daddy" daddy ya xauna kujera yace "Madalla, kowa dai lafiya koh?" Yusuf yace "Duk lafiya" Yusuf bai wani dade ba ya mike yace xai wuce, daddy yace "Baxa ka tsaya mu ci abinci ba" Yace "Alhmdllh daddy na ci abinci" Ammi dake dinning tana jera abincin tace "Anya Yaya Yusuf" dariya yayi yace "Ammi wllh na koshi" tace "Toh shikenan" sallama yyi ma daddy ya fita. Bayan magrib daddy xai je gaida inna babu yanda bai yi da Imaan su je ba ta ki, har hakan ya basa mamaki ya tafi shi kadai, inna na goge tiles din parlonta daddy ya shiga da sallama, ta mike tace "Amma dai gaskiya Bukar ka dinga kwa6a ma yar ka ta daina karya, ce min fa tayi baka dawo ba" Ya xauna yana murmushi yace "Sannu inna, ina yini" ta shimfida tabarma ta xauna tace "Lafiya lau, amma ai karya ba shi da amfani kuma a gaskiya Imaan ta iya karya" Shi dai bai ce komai ba, tace "Toh ya hanyan?" Yace "Alhmdllh mun baro hanya" tace "Wannan karan kuma kamar baxa ka sake dawowa ba" yace "Aiki ne yyi yawa Inna" tace "Toh Allah ya bada sa'a ya tsare mana ku a duk Inda kuke, ya maka albarka" yace "Ameeen inna" Tace "Toh ya xa ayi, Allah ya kaddara a can abincin ka yake, banda haka na tabbata da kana gidan nan da ka dinga share min hawaye daga bakin cikin da nake fuskanta" Daddy na kallonta da mamaki yace "Bakin ciki kuma Inna?" Inna tace "Yo bakin ciki mana Habu... Kaga yayanka baxai fito daga masallaci ya tako nan tun asuban ba ya gaisheni sai ina jin wajen karfe tara xai taho da safe ya duka can bakin kofar ya gaida ni a gurguje ya kara gaba, bana sake ganinsa Bukar sai ina kokarin kulle kofa ta da daddare shi ma Allah yasa ya yi minti biyu xaka ga yace sai da safe daga haka ya wuce, Kaga matar nan tasa Rukayya take ko wa? Uwarsu Mujaheed dai wllh kaji rantsuwar musulmi tafi wata biyu ina ga bata tako ta xo nan ta gaisheni ba sai ta gan ni a tsakar gida ko a can bangaren, ita kuma dayar mai kama da fulanin Bararoji wato Amina da suke ce ma Anty sai ta bushi iskarta xata kwaso kafafuwa ta xo gaisheni, ita wnn farar wa take da suna? Uwar wannan yarinya Imaan d'an wankin da take min da duk ta watsar sun xugeta, in kuwa wannan 'ya taka Imaan borinta ya tashi ta ki kawo min abinci to ranan fa da yunwa xan kwanta a gidan nan, Aisha ta fi karfin ta taso takanas ta kawo min da kanta, to me yafi wannan bakin ciki Yaro? Gashi gaba daya 'ya yanku sun rainani sun maida ni ba bakin komai ba, sun maida ni kakarsu tun ma ba wannan katon Mujaheed ba da ramammiyar 'yar ka, sai wannan kazamar Ummi, ni nasan da sun ga ido wllh taka ni xasu dinga yi suna wucewa, isuhu kadai ke raga min a gidan nan sai wannan yarinya Seeyama, Imaan idan ta fara balbale ni wlh shiru nake, haka ma Mujaheed yaron da aka haifa a gabana, to ina dalili ina da gata na ta ko ina don dai d'an abincin da ake yarfa min a kwano sai a maida ni bola" Daddy dake ta saurarenta ya dago kansa a karo na farko yace "Kiyi hakuri don Allah inna" a fusace tace "Na gaji da jin wnn axxalumin kalman, ayi ta baka hakuri ana cutan ka, ni dai a fita harkata, don idan tsiyata ta debeni wllh sai an fita har kasashen waje ana nemana" Daddy yace "Xa a gyara Inna, duk ki yafe masu, ita Imaan xan sameta yanxu, shi ma Mujaheed din xan gamu da shi" Tace "Atoh, sai ka xaunar da su ka tambayesu kaji ko xaman gidan ne basa son inyi, ka tambayesu dalilin da yasa basa fitsaran su a waje sai a cikin gida cikin gidan ma a kan uwarka, kayi masu jan ido ka nuna masu bacin ranka Yaro" Daddy yana murmushi yace "In sha Allah" nan suka ta6a hira amma kusan hiran gaba daya na complain ne daga karshe daddy yace mata xai wuce masallaci don an kira isha. Daddy na dawowa masallaci ya dinga kallon Imaan dake xaune parlor tana cin abinci, ya xauna yace "Imaan yanxu ita innar kika mayar abar wasar ki a gidan nan?" Kallonsa ta dinga yi kamar zata yi kuka, ya hade rai yace "would you take ur eyes off me silly girl, haka kike ma uwar ki? I warned you the last time a kan haka shine kika sake repeating foolishness din yanxu ko?" Ta sunkuyar da kanta, ya gyada kai yace "Nasan maganin ki, tashi ki bar min parlor" tashi tayi da sauri ba tare da ta bi ta kan abincin ba ta shige bedroom dinta ta kulle, ita dai Ammi bata ce komai ba, Daddy yace "I don't like this nonsense character of her, ita innar abokiyar wasanta ce, ke kuma Aisha baki taka mata burki, a kan me xata dinga rainata, I don't like that, and I am going to teach her manners soon" Ammi ta tabe baki ta mike ta dauke abincin da ta bari ta kai kitchen ta rufe, ta tsaya kitchen din tana wanke plates da ke sink. Washegari wajen karfe bakwai da rabi Imaan ta fito sanye da uniform din islamiyya, kanta a kasa ta gaida Ammi dake jera breakfast a dinning, Ammi dake kallonta tace "Wato ke ba isa a maki fada ba shine kika kwana kuka ido ya kumbura koh?" Ta fashe da kuka tace "Ni Ammi don Allah kar ki sake ce min in kai mata abinci kullum sai tayi ta ma mutum sharri alhalin ba abinda nayi mata" Ammi tace "Ko ban baki abinci kin kai ba ma da kanki naga kike kwasan kafafuwanki kije can din ko da kuwa koranki tayi" Imaan ta hade rai tace "Yesterday was the last day da xan je part dinta, har abada baxan sake xuwa ba" Ammi tace "Toh bari dai ya ji ki gashi can ya fito, ni ba ruwana" shiru Imaan tayi tana juya shayin da Ammi ta hada mata, Daddy dake tsaye parlon yace "Madam me yasa ba a kai ma Inna breakfast ne wai?" Ammi tace "Breakfast kuma?" Yace "Ehh ai ya kama ta ne" tace "A'a don Allah yallabai kar ka hada ni da ita, kullum sai Abba ya tura mata bread, tana da kayan shayi kuma tana da heater ta iya amfani da shi, meye breakfast din dama idan ba shayi da bread ba sai kwai wani lkcn, lunch da kanta tace bata so a daina kai mata wai jagwalgwalon yara ne" Tuni Daddy ya xauna ya sa news channel, Ammi ta shiga kitchen ta ci gaba da abinda take, Imaan ta gama breakfast din ta mike ta iso cikin parlor ta durkusa ta gaida Daddyn nata, sau daya ya kalleta ya amsa ya ci gaba da kallonsa, ta mike ta tafi kitchen ta amshi kudin makarantar ta gun Ammi ta fito ta dau jakarta bayan ta sa takalmi da safa tayi ma daddy sallama ba tare da ta kallesa ba ta fice daga parlon, kiranta daddy yyi ta juyo ta dawo ta sunkuyar da kanta tace "Ga ni" room freshener har biyu ya nuna mata dake ajiye yace "Dauka ki kai ma Inna kafin ku wuce" shiru tayi tana kallonsa kamar xata yi kuka, bata dai ce komai ba ta durkusa ta dauka sannan ta fita xuwa part din inna, Inna na ta goge goge bayan ta gama share ko ina fesss, banda kamshin turaren wuta babu abinda ke tashi a parlon, imaan bata kalleta ba ta ajiye abun hannunta fuska daure tace "Ina kwana" xata fita inna tace "Me ya sami idonki ni Asabe? An umaki wani abun ne" Imaan da har ta kai kofa ta juyo lkci daya ta fara kuka tace "Kawai sai kije kice ma daddy ina maki rashin kunya yaushe rabon da in xo nan...." Tana fadin haka ta fashe da matsanancin kuka, Inna da ta saki baki tace "Shine ya maki me?" Cikin kuka tace "Fada ya dinga min mana yace zai yi magani na" Inna ta dau dankwalinta ta fita parlon imaan ta bi ta da kallo tana share idonta, Ko sallama babu inna ta bude kofar parlon, daga daddy har Ammi suka daga kai suna kallonta, tace "Bukar dama yaro ba lallabasa ake yi ba a rayuwar nan, daga mun yi magana tsakanina da kai sai ka taho ka far ma yarinya da bala'i, to ae gwara ita sau dubu a kan sauran, Imaan bar ta da son jikinta amma wllh wllh bata da matsala, haka kawai ka ja mata wani cutan dama gata mai cuta iri iri kamar ta kashe d'an mutum, yanxu da kasa ta kwana tana kuka idan wani abun ya sameta me xa ka gaya ma Allah, kai dai wllh ka cika bala'i, ba haka yayanka Ahmadu yake ba, ba ruwansa da irin wannan hali, to wai ma me ta min da xafi haka da xaka sa ta kuka haka, ga abun duka can Mujaheed me nuna ni da yatsa, mai ce min Hajiya, ni tunda nake wllh xan iya kirga sau nawa Imaan ta mayar min magana shima kuma duk laifina ne....." Ammi dai tuni ta shige kitchen, Daddy kuma ya kasa cewa komai, Inna ta juya ta nufi kofa tana cewa "Wannan dai ba yi bane, kamar ba kai ka haifeta, yar gata daga ita sai ita amma kuma ka takurata, da wanne xata ji da rashin karo mata kanni da ba ayi ba har yau ko kuma da fitinar mahaifinta, kuma ka tashi ka kawo min turaren bature da ko kamshi babu wai in fesa a daki, to uwata bata ce min je ki kya gani ba turaren wuta tsadadde mai kamshi nake nufi, sai ka ba matarka mai kumewa a daki kamar matar liman ta fita kasuwa ta siyo min" daga haka ta fice ta kulle masu kofa. Dama imaan direct gun mota ta nufa bata yarda ta ma bi ta part dinsu ba. Yusuf ne ya ajiye su islamiyyar, karfe sha biyu Anty ta dauko su, A hankali Imaan ta bude kofar parlonsu tana lekan ciki, babu kowa hakan yasa ta shiga ta rufe kofar ta nufi bedroom dinta da sauri, tana kokarin cire Uniform dinta Ammi ta bude kofar, Imaan ta gaisheta kanta a kasa, Ammi tace "Amso min card waje kafin ki cire uniform din" Imaan ta amsa tana kallonta tace "Ammi daddy fa?" Ammi tace "Yana daki" Imaan ta marairaice tace "Ni fa ban gaya ma inna ya min fada ba, kawai taga idona ne haka" Ammi tace "Wannan ya rage naku ke da shi, ni kiyi sauri ki amso min card din" imaan ta maida Hijab dinta ta fita, kiosk din is just a house from theirs, ta amso card din ta juyo ta shigo gida, Umma ta gani tsaye parking space alamar xata fita, Mujaheed ya iso wajen ya bude mata back seat, sannan ya shiga driver seat, Imaan na hada ido da Umma dama ta dauke kai tayi wucewarta, Mujaheed ya bi ta da kallo ta madubi, Umma ta shiga cikin motar tace "Wllh duk ranan koda ka gaida uwar yarinyar nn ko da mistake a gidan nan ban yafe maka ba Mujaheed, duk kanninka ma na karanta masu haka nasan kuma sun dauka...." Yana kallonta ta madubi yace "Haba Umma kema kin san....." Ta karasa masa da sauri tace "Baxa ka iya ba ko? tunda ga ta kanwar Ahmad ko kanwata, Mara tunani kawai da bai san ciwon uwarsa ba, to mu xuba da kai wllh, ba dai makiyana su ne mutanen arxikin ka ba a gidan nan, ka ci gaba, a ta dalilin munafukar uwar yarinyar nan na bar gidan ubanka for good 5 years, ta hade kai da kishiyata suka yi ta kulla min makirci har ubanka ya sakeni, da yake akwai sauran xamana a gidan na dawo few years back na tarar baka da masoya da ya wuce makiyana, ka maida Aisha uwarka, ka nuna duk gidan nan baka da kanwa da ya wuce yarinyar Aisha, yarinyar da bata gaisheni a ynxu ko idona xai makale a nata saboda uwar ta hanata, da kyar da siddin goshi da rokan Allah na rabaka da su, ni da ba a kan idona na haifeka ba kuma ina haihuwar ka aka ajiye min kai a gefe na da wllh bbu abinda zai sa baxan ce canjen ka aka min a asibiti ba, sam baka san mutunci na ba, ace makiyana su ne masoyan ka Mujaheed? Anya kana son gamawa lfya kuwa?" Shi dai ya kasa cewa komai, ta gyada kai ta bude motar ta fice tana cewa "Ga ka ga su ai, daga ynxu ma ka tatttara yanaka yanaka ka koma bangaren nasu" a hankali yace "Umma I have avoid a lot of things a gidan nan kema kin sani, wllh ko kadan bani son abinda xai bata maki rai, don Allah kiyi hakuri...." Ko saurarensa bata yi ba ta fice daga compound din ya sauka ya bi bayanta da sauri. Washegari har Ammi ta gama hada breakfast ta fito daga kitchen imaan bata fito daki ba, ta kalli agogo ganin bakwai da quarter ta nufi dakin ta bude ta shiga, kwance ta ganta ta dukunkune cikin bargo, Ammi ta karasa da sauri ta cire bargon tace "Are you okay Imaan?" Ta bude ido kamar xata yi kuka, Ammi ta dinga kallonta don jikinta ya dau xafi sosai, a hankali tace "Ina ke maki ciwo kuma?" Kafafuwanta ta nuna mata da kai, hawaye cike idonta tace "Ammi duka jikina ciwo, jiya ban yi bacci ba" Ammi ta kamo hannunta cikin sanyin murya tace "Ba ki sha magani ba jiya da daddare ko daughter" ta nuna ma Ammi magungunanta a side drawer tace "Na sha Ammi" saketa Ammi tayi ta mike ta shiga bathroom ta hada mata ruwan wanka ta fito tace "Toh shiga kiyi wanka sai ki kara shan maganin" da taimakon Ammi ta sauka kan gadon, Ammi na rike da ita suka shiga bathroom, bayan ta wanke baki Ammi ta taimaketa tayi wanka ta fito, barin ta tayi ta sa kaya ta tafi hado mata shayi, Daddy na xaune parlor yana dube dube a laptop, ta tsaya bayan kujerar tace "Yallabai jikin imaan fa kar ya rikice mana ko xa aje asibiti tunda likitan ma baya nan" daddy ya mike yace "Bata jin dadi ne" Ammi tace "Nima yanxu na shiga ganin bata fito ba, her temperature is high tace bata yi bacci ba" daddy ya d'an yi shiru, Ammi tace "Kwanakin baya ciwon ya lafa sosai, as from some weeks ago yanxu duk sai ya tasar mata ga xaxxabi da ciwon kai kuma tana shan drugs dinta" Daddy yace "Toh ta shirya mu tafi asibiti" Ammi tace "Toh" komawa yayi ya xauna, ita kuma ta wuce dinning don hada mata shayi. Kwance ta sameta bayan ta sa abayar da ta fiddo mata, da kyar Imaan ta sha shayin, Ammi ta fesa mata turarrukan ta ta bata veil din abayar sannan suka fito parlor, kwanciya tayi kan kujera tana gaida daddy dake rike da makullin mota yana jiransu, ya amsa yace "Sannu mamana, tashi mu je to" mikewa tayi ya kama hannunta suka nufi kofa Ammi na masu Allah ya kiyaye hanya, A hanya daddy ya hadu da Abba ya taho daga part din Inna, gaisawa suka yi, Imaan ma ta gaishesa a hankali, Abba yace "Jikin ne ya tasar mata?" Daddy yace "Wllh kuwa, xa mu je asibiti ne yanxu" Abba yace "Subhanallah tana shan magunguna kuwa" Daddy yace "I think so" Abba yace "Toh likitan ta fa?" Daddy yace "Yayi tafiya ne" Abba yace "Toh tunda Muhammad na nan ba sai ya dinga dubata ba kafin likitan nata ya dawo, ko gwara a tafi asibitin?" Daddy yace "Noo in xai dubata shikenan, dama don likitan baya nan ne xa mu je asibitin" Abba yace "Let me give him a call, na barsa sashin inna, idan ma asibitin xa a sai ya kai ta kawai" Yana kokarin kiran Mujaheed suka hangosa yana tahowa, Abba ya maida wayarsa, har Mujaheed ya isa parking space da suke tsaye kallonsu kawai yake, Ya risina ya gaida Daddy, ya amsa masa da fara'a, Abba yace "Imaan xaka duba Mujaheed, bata jin dadi" Sosai gabansa ya fadi ya kalli Imaan dake jingine da mota duk ta wani langwabe. I appreciate my fan's love always, ina yinku fisabilillah😘😍🌟⭐ *Imaan* ⭐🌟 _By khaleesat Haiydar_✍🏻 5..... Gaba daya Mujaheed ya daburce ya rasa abin cewa, Abba yace "Ko in kai ta asibitin kawai" da sauri yace "Noo Abba, naga bani da kayan aiki a gida ne, sai dai in kai ta asibitin in duba ta a can" Abba yace "Toh hakan na da kyau" Magana yake amma gaba daya rabin attention dinsa na kan window din dakin Umma duk da baya hango komai, amma fatansa yanxu ace bata tashi bacci ba duk da yasan da wuya, Ya sunkuyar da kansa yace "Toh xan dauko makullin mota a ciki" Daddy ya mika masa nasa makullin motar yace "You use my car, duk yanda ake ciki you let me know" Mujaheed ya risina ya amsa makullin motar yace "Toh Abba" daddy yayi ma yayan nasa sallama ya wuce ba tare da ya kalli imaan da ta cika saura kiris ta fashe ba, bayan ya tafi Abba ya kalleta yace "Sannu Mamana" Ganin hawaye idonta yace "Baki son bin Muhammad din kenan?" Da sauri ta gyada masa kai hawayen na sakkowa idonta, yace "Kuma baki son daddyn naki ya huta koh, am sure kila xuwa anjima ko gobe xai koma bakin aiki, shi Mujaheed din ba yayanki bane?" Ta fashe da kuka tace "Abba ihu xai ta min a hanya fa" Abba yyi murmushi mai sauti sai dai bai ce komai ba, Mujaheed dai sai kallonta yake ta gefen ido, Back seat Abba ya bude mata yace "Shiga" a hankali ta shiga ta jinginar da kanta jikin motar, Abba na kallon Mujaheed yace "You take very good care of her, ko kallon banxa ban yarda kayi mata ba" Ya sauke idonsa yace "Toh Abba" Abba ya daga mata hannu ta mayar masa tana goge idonta, ya juya ya wuce ciki, Mujaheed ya gama warming motar yayi horn ana bude masa gate ya fita gidan, sai da suka hau saman titi yace "Saboda baki son xuwa schl shine kika fake da ciwon karya salon ki ba mutane wahala koh?" Jin bata ce komai ba ya kalleta ta madubin motar, murguda masa baki take, suna hada ido ta turo bakin kamar xata yi kuka sai dai bata ce komai ba, ya gyada kai yace "Xaki gwammace schl kika yi tafiyar ki yau" ta fashe da kuka tace "Dama dai Abba yace duk abinda ka min in gaya masa" Bai tanka ta ba har suka iso asibitin da yake aiki, yana gama parking ya bude motar ya fita ita ma ta fita, ya rufe motarsa ya dau hanyar entrance din shiga hospital din, a sauri ta bi bayansa, tsaye ta gansa reception suna gaisawa da nurses dake wajen da fara'a, Wata nurse tace "Doctor I heard an sake transferring dinka xuwa nan, kuma shiru ba mu ganka ba" Yace "Sure da yau xan yi resuming, but due to some reasons sai Wednesday in sha Allah" duk nurses din suka amsa masa da Allah ya kai mu, juyawa yyi yaga Imaan ta nemi kujera tayi xamanta, wata nurse tace "Dr sister dinka ce?" Yace "Sure bata da lafiya ne" daga haka ya wuce sama, duk sai da ya shiga office din doctors dake duty safiyar, Dr Mukhtar na ganinsa ya mike yace "Kaga mara kirki dama yau xaka yi resuming shine babu sanarwa" Mujaheed ya karasa yana murmushi suka gaisa yace "Sai Wednesday in sha Allah, na kawo sister na ne bata da lafiya" Mukhtar yace "Subhanallah Ummi ko Rahma?" Yace "None, cousin dita ce wannan" Dr Mukhtar ya koma ya xauna yace "Ohk tana ina" Yace "Tana reception" Dr Mukhtar ya buga waya downstairs ba a dau lkci ba wata nurse ta shigo office dinsa, gaida Mujaheed tayi da fara'a ya amsa yace "Ya aikin Zainab" tace "Alhmdllh Dr" Dr Mukhtar yace "Ki taho da patient dake reception" tace "Wanne they are almost 7 patients downstairs" Mujaheed yace "Imaan sunanta" tace "Ohk" daga haka ta fita, tare suka dawo da Imaan da ta wani yi laushi da kyar take jan kafar, Dr Mukhtar ya nuna mata kujeran dake kallon wanda Mujaheed ya xauna, ta xauna xata kwantar da kanta kan table Mujaheed ya mata wani kallo yace "Tashi" kamar xata yi kuka ta dago kanta, likitan yace "Sannu Imaan, ya kike jin jikinki, like ina ke maki ciwo?" A hankali tace "Jiya da daddare bayana ya dinga min ciwo har da kai na kuma ina jin sanyi, ban ma yi bacci ba" likitan yyi murmushi yace "Yau da safe fa" Ta kallesa murya can kasa tace "Kafafuwana suka fara min ciwo da na tashi, anjima kuma duk jikina ya fara min ciwo" Ya langwabar da kai yace "Ikon Allah, suna maki haka ne?" Kai ta gyada masa, yace "Toh kina shan wasu magunguna ne?" Kai ta gyada masa, yace "Kin san sunan su?" Ta gyada masa kai, yace "Can you write them down for me now?" Tace "Sure" farar takarda ya ajiye mata da pen, nan ta rubuta masa gaba daya drugs dinta har da na shafawa ta mika masa takardan ya amsa yana dubawa, bayan few seconds ya daga kai yana kallon Mujaheed dake kallonsa shi ma, kafin yace komai Mujaheed yace "Rubuta mata injections taje ayi mata" Likitan yyi yanda Mujaheed yace, Mujaheed ya amshi takardan yana kallon alluran da ya rubuta mata sannan ya mika ma Imaan da ta kife kanta da table yace "Karba kije nurses su maki alluran" ta dago da sauri tace "Yaya allura kuma, ni doctor na baya min allura magani kawai yake ban" ya jefa mata wani kallo yace "Sai ki jira ya dawo ya ci gaba da baki maganin, nan kam allura xa a maki, get up my friend" a d'an tsawace ya karasa maganan, Ta amsa lkci daya hawaye ya cika idonta ta juya ta fita office din, a hankali Dr Mukhtar yace "Is she a sickled cell patient Mujaheed?" Mujaheed ya girgixa kai yace "Not at all, She is only carrying the trait, a carrier" da mamaki Likitan yace "But it's almost mimicking the disease" Mujaheed ya buda hannu yace "Mu ma haka muka gani" Dr Mukhtar yace "Subhanallah, this is kind of rare, Allah ya bata lafiya" Mujaheed yace "Ameen" Dr Mukhtar yace "Kasan alluran are strong, ta ci abinci kuwa?" Mujaheed ya mike da sauri yace "I don't know, bari in tambayeta, kafin in dawo plss kayi prescribing drugs in addition to hers" daga haka ya fita, injection room ya shiga bayan nurses din sun sanar masa suna ciki xa a mata alluran, tsaye take tana hawaye nurse din ma na tsaye rike da alluran sai kallonta take, tana ganin Mujaheed tace "Yauwa Dr ta ki fa" Mujaheed ya hade rai yace "Are you a baby? Waye kike son ba wahala, xan maida ki gida da ciwon ki ne idan baki yi respecting kan ki ba" ta fashe da kuka bata ce komai ba, Yace "Kin ci abinci?" Cikin rawar murya tace "Na sha shayi kadan amma yunwa nake ji" wani kallo ya dinga mata, can ya kalli nurse din yace "Nurse let me get her something to take plss" nurse din tace "Ba damuwa Dr" daga haka ya fita, nurse din ta nuna mata kujera ta xauna. Rike da malt Mujaheed ya dawo injection room din, ya bude sannan ya mika mata, Kadan ta sha xata ajiye yace "Wa za ki ajiye ma" ta hadiye na bakinta da kyar tace "Xan sha idan an gama min" nurse din tace "Aa ki kara kadan" da kyar Imaan ta kara malt din sannan nurse din tasa ta tashi, ta mike ta fashe da kuka tana kallon Mujaheed tace "Wllh tsoro nake ji xai min xafi" nurse din tace "Baxai maki ba kuwa" Mujaheed yace "Xan fa tafi in bar ki a asibitin nan kina bata min lkci" tace "Don Allah kai ka min plsss" yace "Baxan yi ba, kin tsaya ko inyi tafiyata" da kyar ta isa kusa da nurse din, ta kallesa ta mika masa hannu jikin rawar murya tace "Don Allah ka rike min hannu Yaya" bai san lkcn da yyi murmushi ba ya karasa inda suke, ta kama hannunsa ta runtse ido, nurse din tace "Me yasa baki sa under skirt ba?" Ta turo baki tace "Ni bana so" nurse din tayi murmushi, ta daga mata abayar jikinta, rungume Mujaheed tayi ta kwantar da kanta kirjinsa, cikin rawar murya tace "Wayyo Yaya don Allah kace ta min a hankali, kar ta min da xafi" Mujaheed ya amshi alluran hannun nurse din yayi mata, xaro ido tayi tana cewa "Yaya ta sa alluran? Don Allah tayi a hankali, tuni ya amshi dayan alluran yyi mata shi ma, sae da ya cire syringe din ta sakar masu ihu duk tunaninta lkcn xa ayi alluran, ya turata daga jikinsa, ta dinga xaro ido, nurse din tayi dariya tace "Toh ba gashi har an gama ba" Imaan ta zaro ido tace "Da gaske? To ban ji sanda aka cire ba" Mujaheed dai ko kallonta bai yi ba yyi disposing syringe din ya nufi kofa, nurse din tace "Ki fa danna wajen sosai idan kun koma gida" Imaan ta gyada mata kai tana goge idonta har sannan tana mamakin wai har an mata allura don bata ji zafin da take ta jira ba, ta dau sauran malt dinta ta fita, xaunawa tayi reception ganin bata gansa ba, bayan kusan minti goma sai gashi ya sakko, yana kallonta ya nufi kofa, da kyar ta mike tace "Yaya na fara jin jiri" yace "Toh ko in bar ki a nan" da sauri ta girgixa masa kai ta isa gunsa, saura kadan ta fadi gun fita, ya kalleta sau daya yyi gaba, back seat ta shiga ta kwanta tana maida numfashi, ya shiga motar ya tada suka bar asibitin, wani pharmacy ya tsaya xai fita tace "Yaya wllh idona juya min yake" nan ma dai bai tanka ta ba, drugs dinta da sabbin da Dr Mukhtar yyi prescribing ya siya mata sae lucozade boost babba biyu, duk ya ajiye bayan motar, har suka isa gida yyi parking a parking lot din daddy bacci Imaan take, daga cikin motar ya dinga lekan apartment dinsu gabansa na faduwa, ya juya ya kalleta, sannan ya fito daga motar, ya bude back seat yace "kee" bude ido tayi da sauri, yace "Sakko" ba musu ta fito daga motar da kyar, ya dau magungunan da drinks din ya rufe motar, da sauri ya juya ganin kiris ya rage ta fadi ya kara kallon apartment dinsu, kamo hannunta yyi ta jingina jikinsa. Har suka isa bangarensu, ya bude kofar ya shiga parlon hade sallama, Imaan ta kwanta saman kujera ya ajiye drugs din hannunsa da lucozade boost ya kalleta kafin yace komai daddy ya fito parlon, yace "Har kun dawo kenan?" Mujaheed yayi kasa da kai yace "Eh mun dawo Abba" dukawa yyi ya dau ledan maganin ya fiddo gaba daya, ya bude wanda xata sha a lkcn yana kallonta yace "Tashi ki sha magani" Daddy ya tafi kitchen don dauko table water da cup, Mujaheed daure fuska kamar tana ganinsa yace "Baxa ki tashi ba?" A hankali ta bude ido ta mike xaune kamar xata yi kuka, daddy ya iso parlon ya ajiye ruwan da glass cup yace "So how much is the bill doctor" kallonsa Mujaheed yyi, sai kuma yyi murmushi yace "Bill kuma Abba" Daddy yace "Eh ba asibiti ku ka je ba, ga kuma drugs ka siyo" ya girgixa kai yace "A'a Abba, I have settled everything, Allah ya bata lafiya" daddy yace "Toh madalla, Allah ya yi albarka" Mujaheed ya debi ruwan ya mika mata tare da drugs din ta amsa, tana runtse ido ta kai baki sannan ta sha ruwan, mikewa Mujaheed yyi yace "Xan koma daddy Allah ya bata lafiya" Daddy yace "Ameen thanks Son" daga haka ya fita parlon, daddy na kallonta yace "Toh tashi ki shiga ciki ki kwanta" ba musu ta mike ta wuce bedroom dinta. Mujaheed na shiga parlonsu ya kalli mahaifiyarsa dake sakkowa downstairs, kai kana ganin shirin da tayi kasan fita xata yi, Anty dake parlor tana kokarin sa turaren wuta a burner ta kalli Mujaheed tace "Har kun dawo kenan, ya jikin nata?" Gabansa ya fadi sosai, ya hadiye abu da kyar yace "Eh na dawo" Anty tace "Daxu Abban ku ke gaya min ka kai Imaan asibiti, da naga breakfast dinka baka yi ba" kasa cewa komai Mujaheed yyi, ya d'an saci kallon Umma da ta tsaya stairs tana kallonsa baki bude, Anty tace "Ji walakanci ba da Mujaheed nake magana ba" Da kyar yace "Anty ba fa ni na kai ta ba, Abbanta ne ya kai ta" Shiru Anty tayi ganin yanayinsa, can ta saci kallon inda yake kallo, d'an tabe baki tayi ta duka ta ci gaba da abinda take, Umma ta juya ta koma sama, da kyar Mujaheed ya ja kafarsa xuwa dinning, har Anty ta gama abinda take Mujaheed na xaune bai taba komai a dinning table din ba, tace "Idan baka ci ka kai min su kitchen a ba almajirai" ya marairaice yace "Anty da baki yi magana a gaban Hajiya ba" Anty ta maka masa wani kallo tace "tunda uwata ce ita ba" Bai ce komai ba, bayan wani lkci ya mike ya fita parlon ko a mafarki bai ma son haduwarsa da Umma, to me ma xai ce mata ta yadda, part din Inna ya nufa, ya sameta xaune kan tabarma rike da cazbi tana ta xuba gyangyadi, kwanciya yyi kan kujera ya lumshe ido, inna ta yi gyangyadin ta mai isarta sannan ta bude ido, a tsorace ta koma baya ganin sa tace "Meye wannan?" Shi dai bai tanka ta ba bai kuma bude ido ba, tace "Wannan dai ba yi bane ina Lazimi kato ya fado min parlor ba sallama" Ba tare da ya bude ido ba yace "Kina gyangyadi dai" rai bace tace "Ya xaka ce ina gyangyadi ga carbi hannuna, ai asararre ne xai yi gyangyadi a wannan lokacin walha fa na gama ina lazimi ka shigo sadaf sadaf ban sani ba" Mikewa xaune yyi yace "Akwai ruwan shayi?" Tace "Eh akwai wanda uwarka ta kawo min" ya kalleta bai ce komai ba, tace "Can din hanaka ruwan shayin suka yi?" Komawa yyi ya kwanta, tace "Sai dai in sa Aisha ta dafa maka don baxan iya ba, baka ji bayana ba tun safe nake aiki, ko kai baka ga ko ina fess ba, leka dakina ma kaga yanda yake talli" shi dai bai ce mata komai ba, tace "Duk na tattara ma yarinyar nan me shigo min daki ta kwanta ta bar min tsummokaran dankwalayenta idan ta tashi tafiya, suna can baranda na ajiye mata, sai kaga hasken da dakin yyi wllh, ni dai da xata taimaka ta daina shigar min daki don Allah, ni tsoron da nake jiye mata idan tayi aure, ko ina fa ta samu barin kayanta take kamar mahaukaciya, Bukar dai ya haifo abinda ya fi karfinsa" mikewa Mujaheed ya sake yi ya shiga kitchen, ba a dau lkci ba ya fito rike da cup din ruwan xafi yace "Ina kayan shayin?" Makulli ta kunce a habar xaninta ta mika masa tace "Saboda ire iren su Imaan nake adana kayana, ba ruwana" Ya tabe baki ya amshi makullin ya shiga dakinta, closet dinta ya bude yaga gwangwanin madara manya har biyu da milo biyu sai kwalin sugar uku, da kwalin lipton girgixa kai yyi ya sauke madaran da Milo, muryarta yaji a bayansa tace "Da dai ka bari in xuba maka Mujaheed kada ka min barna" Wani kallo ya mata, ya debi cokalin Madara har uku ya xuba, ta bude baki cikin tsawa tace "Kai ubanka ne ya siyo min xaka diba haka, Bukar ne dai mai siyo min kayan shayi, shi Ahmadu sai dai ya jibge min kayan abinci kamar mayunwaciya, kudin nan fa da wahala ake samun su" shi dai bai tanka ta ba har ya gama hada shayin sa ya fita, tayi kwafa ta kwashe kayanta ta maida closet din ta kulle da makullin tana cewa "Ae dai gobe rana ce" Daga haka ta fito parlor. Har kusan azahar Mujaheed na bangaren Inna, har ya gaji da jin muryarta gashi bai taho da earpiece balle ya toshe kunnensa ba. Yana kokarin tashi ya je yyi alwala jin an kira sllh aka bude kofar parlon ya kalli kofar da sauri, Imaan ta shigo parlon rike da warmer, har ta rame ciwon kwana daya sai manyan idanuwa, Inna ta saki baki tace "Wacece wannan kuma?" Imaan bata ko kalleta ba ta ajiye warmer din hannunta, inna ta rike ha6a tace "Ni dai naga abinda ya isheni bai ishi ubangijina ba, yanxu fa sai ace jikinta ne ya tashi, fisabillah dubi yanda yarinya ta zabge ta koma fiyot kamar kyanwa Mujaheed, anya iyayenki na son ki kuwa yar nan, haka xasu xuba ido suyi ta kallonki kina wahala ga magani kasadan na wani malami a Maiduguri ance min babu ciwon da baya warkarwa, dubu hamsin aka ce xa a basa Bukar ya maida ni ban san abinda nake ba kamar shi ya haifeni, ta rasulu kawata xata cuce ni ne ake tunani? ce min fa tayi xata min hanyar samun maganin don can bayan tsauni mutumin yake, kuma babu kalan iskan da bai warkarwa da ciwace ciwacen da ba na Allah da annabi ba irin na yarinyar nan, amma iyayenta sun ba tsinannun turawa karfi sun amince masu dari bisa dari ba saurarana xa su yi ba, dubi don Allah yanda ta fige, lafiya muka rabu jiya amma ga iskan har ya tashi tunda gashi bata je makaranta ba" Mujaheed yace "ina kika ce mai maganin yake" Inna ta gyara xama tayi kasa da murya tace "Wllh a bayan tsauni ta rasulu tace yake, sannan aikinsa yanda kasan yankan wuka, sha ynxu maganin ynxu, duk xata fitsare ciwon da iskan inji ta rasulu" yyi murmushi yace "Ikon Allah, boka ne kenan?" Buda baki tayi tace "Kaji salu6a66e ko, ni dai ka rufa min asiri kar ka ja min kasa Ahmadu ya kafa min sabon babin wa'axi, kai ynxu fata kake inje wajen boka d'an nan" yace "Atoh, mutumin kirki dai baxai je bayan tsauni ya xauna ba" tace "Yo ai ni ce gantalalliya ma da nake xancen nan da kai na mance ashe d'an aiken turawan ne kai ma, Allah wadaran naka ya lalace, ba damuwa ni da ya xame ma dole xanje samo mata magani kuma kada wani shege ya min maganan banxa, Allah kuma ya tsine ma turawan nan dai" Imaan dake tsaye bakin kofa har sannan ta tabe baki tace "Kar ma ki amso ni baxan sha ba, daddy yace min in daina hada na asibiti da gargajiya" a fusace Inna tace "Kya tsufa a gida ina kallonki kina kallona don wllh babu namijin da xai auri ciwo da kudinsa ki karar masa da tattalin arxiki a asibiti, wllh baxan bari a cucesa ba duk sai na xayyane masa lalurorin ki don ni ba yar cin amana bace, ni yar gaskiya ce, ke ce ciwon kafa, kece ciwon baya, ke ce ciwon kai, ke ce ciwon mara, kece sanyin k'ashi, kece xaxxabi, kece ciwon jiki, ga shegen son jiki sannan in rufe masa da cewa duk iska ne da ba a san kansa ba, ba ruwana wllh" murmushi Mujaheed yyi ya mike ya fita don yin alwala, Imaan ta mata wani kallo bata son magana saboda daddy ta juya kawai ta fice mata daga parlonta tana murguda baki. I am soo grateful for the birthday wishes from families, friends, fans, and love ones, Allah bar xumunci ya kara mana shekaru masu albarka.🌟⭐ *Imaan* ⭐🌟 _By khaleesat Haiydar_✍🏻 6..... Hatta islamiyya Imaan bata iya taje ba ranan banda bacci babu abinda take, xuwa lkcn jikin ya mata sauki sai dai rashin kwari, Daddy dake parlor a study area dinsa ya kalli Ammi dake parlon ita ma yace "It's almost six madam baxa ki tada Imaan ba?" Ta kallesa tace "Kafin magrib xan tasheta" yace "Amma jikin ba xafi koh?" Tace "Ehh ba xafi but she's weak" yace "Allah ya bata lafiya" a hankali Ammi tace "Ameen" bayan wani lkci ta kallesa tace "Am really disturbed with Imaans health ailment... She have suffered a lot but always claiming strong, and...." Sai kuma tayi shiru, a hankali ta ci gaba "I don't want to loose her" Daddy na kallonta yace "Allah plans best, ke dai ki ci gaba da yi mata addu'a a ko da yaushe wataran sai labari, Allah xai yaye mata" Ammi tace "In sha Allah" Bayan magrib Ammi na kitchen taji muryar inna a parlor, fitowa tayi ta gaida ta da ladabi tace "Sannu da xuwa inna" inna tace "Ina mijin naki?" Ammi tace "Ya fita masallaci" Inna tace "Daxu Imaan ta xo duk tayi wani fayau fayau da ita, jikin ne ya matsa mata koh?" Ammi tace "Ehh wllh, amma taji sauki ma yanxu, tana daki xata yi sllh" Inna tayi kasa da murya tace "Yanxu 'yar nan idan shi mijin nan naki boko ya gama cutarsa ya ratsa sa ta ko ina ke baxa ki maida hankali ki tashi tsaye kiyi ta kanki da 'yar ki ba? Fisabillilah meye laifin maganin gargajiya Aisha, komai sai ace sai asibiti ga na gargajiya kasadan?" Ammi tace "Gaskiya ne inna" Inna tace "Wllh malamin a bayan tsauni yake" Ammi ta d'an bude ido tana kallonta, tace "Ga aikinsa kamar yankar wuka, duk xata fitsare jaraban ta dawo kamar mutane, amma ni tsoron magana nake Bukar da Ahmadu ba kirki ne da su ba sai su karee min rashin mutunci suce boka ne alhalin ba boka bane kawai Allah ne yyi xamansa a bayan tsauni, ta rasulu ta sha xuwa can kuma ana kwana daya da rabi a hanya kafin a kai, tunda kika ji haka ai kinsan akwai kamshin nasara, tafiyar kwana daya har da rabi ai kuwa akwai nasara....." Shigowar Daddy ya sa tayi shiru, daddy ya gaida ta da ladabi ta amsa masa sama sama tana kallon Ammi tace "Kina ji 'yar nan bari in koma na bar kofa bude kada yaran gidan nan su min aika aika ga dambun nama ta can daki, dama Mujaheed sai xarya yake min tun safe, ko shi ya isa ya kwashe, yanxu dai yaushe mijin naki xai koma?" Ammi tace "Xuwa gobe in sha Allah" Ammi tace "Toh idan ya tafi ki taho sashina ki same ni mu karasa maganar a can don sirri ne" daga haka ta nufi kofa daddy na mata sai anjima ko tanka sa bata yi ba. Bangarensu Mujaheed inna ta nufa tana cewa "Ita kuma Amina bara inje inji ko lafiya ban ganta yau ba" Mujaheed ne xaune parlor sai Yusuf, Hajiya na dinning tana jera abinci Rahma na taya ta, gaba daya Mujaheed bai yarda sun hadu ranan ba sai yanxu da ta riskesa a parlor ta fito kitchen, Inna na kallon Yusuf tace "Kai ina uwar ka, lafiyarta yau bata xo gaisheni ba" Yusuf yace "Yanxu da daddaren nan xaki kamo hanyan xuwa nan inna" Hajiya ta karaso parlon tayi kasa da kai tana daga tsaye tace "An yini lafiya Inna" Inna tace "Rukayya idan Hadiza ce xa ki gaida ta a tsaye sandandan haka?" Juyawa Umma tayi ta koma ta ci gaba da abinda take ba tare da ta bata amsa ba, inna ta kara da cewa "Sannan kiyi min rai ki rufa min asiri ki daina gaisheni kwata kwata a gidan nan idan kin gan ni, don Allah bana bukata, wnn ae kanki kike munafurta, kuma Allah ya tsine ma gaisuwar" Wani kallo Mujaheed ke ma inna fuskarsa daure, inna tayi kwafa tace "Mu xuba dai, xamu ga mai kwashewa, ae kema ga naki d'an ya isa aure ba don ya tsaya shashanci ba xaki ji ko da dadi ko babu" mikewa Mujaheed yyi yace "Ke dai ba dai alkhairi ya kawo ki nan ba sai fitina da complaint, haba don Allah, gaba daya ba a ta6a maki dai dai...." Inna ta bude baki tace "Ni kake xagi Mujaheed?" A fusace yace "Mu bar sa a hakan" daga haka ya wuce ta kamar xai tashi sama, Yusuf ya bi sa da wani kallo, tuni Umma ta shige kitchen ranta fari fat duk da haushinsa da take ji, Yusuf ya mike yace "Yi hakuri muje in raka ki" Inna ta fara matsar kwalla tace "Isuhu kaga abinda Mujaheed ya min ko? Da ina kusa da shi babu mai hanasa make ni.... Ina mahaifin ku yake" Yusuf yace "Ke dai mu je, Abba bai dawo ba" Da kyar Yusuf ya lallabata suka fita parlon tace "Wllh in har Mujaheed zae ci gaba da xaman gidan nan sai dai ni in tafi" Yusuf ya danne dariyarsa suna isa part din su Imaan ta bude kofa, daddy dake xaune yana duba laptop ya mike ganinta tace "Bukar babu abinda Mujaheed ya mance bai gaya min ba yanxun nan daga nayi ma uwarsa gyara, sai ku xaba ko ni ko shi a gidan nan" daga haka ta rufe kofar. Yusuf dai tuni yyi gaba, suna isa part dinta ta rushe da kuka tace "Sai yanxu abun ke min ciwo isuhu, kai kaga wahalar da nayi da Mujaheed kare baxae ci ba wllh" Yusuf yace "Sai kiyi hakuri, Mujaheed din ki ne fa" a fusace tace "Mujaheed dinsu dai, bari dai mahaifin ku ya dawo xai gaya min ko shi ke koya masa ya min rashin arxiki" kiran Isha da ake yasa Yusuf ya bar part din inna, tare Daddy ya je gun Inna da Imaan bayan isha, Inna ta fito daga daki ta shimfida tabarma ta xauna tace "Wllh Bukar daga nace ma Rukayya ta daina gaisheni a gidan nan don na munafurci ne, shi kenan Mujaheed ya hayayyako min yana huci..." Daddy yace "Kiyi hakuri Inna, ina fita xan je in samesa yanxu" a fusace tace "Oh oh babu xancen samunsa, kawai ni ba na son ganinsa gidan ne ko kuma ni in tafi ai dama ya isa aure sai yyi ya koma gidansa baxan xauna tare da shi wataran ya mareni ba, wai ku me yasa baku san ciwon uwar ku ba, uwarsa fa na yi ma fada shine ya min rashin arxiki haka, kai ko ga ka xaune sandandan gabana kana bani hakuri, ya fi karfin ka ne mujaheed din ko kuma uwarsa ta fi naka ne, Ahmadu dai bai ba yaron tarbiyar da ya ratsa jikinsa ba wllh" Daddy ya mike yace "Xan dawo anjima inna" daga haka ya nufi kofa tace "Yauwa, ka titsiye sa sai ya gaya maka ko ni sa'arsa ce kafin ya bar gidan" shi dai bai ce mata komai ba har ya fita, Inna tayi kwafa tace "Xai san ya ta6a uwar su yau" Imaan dai na kwance kan kujera tana kallonta, Inna tace "Ni na ma fara tsoronsa tunda abinda ya zama kenan yanxu" Imaan tace "Toh ke me ya kai ki bangarensu" inna tace "Ya za ki ce min haka 'yar nan, ni da gidan d'a na kuma kice me ya kai ni?" Imaan dai bata ce komai ba, Inna tayi kwafa tace "Ke kin ga wahalar da nayi da Mujaheed?" Imaan tayi dariya tace "Ae ke dama kullum sai kice kin yi wahala da kowa" Inna tace "Kee na Mujaheed k'are baxai ci ba, ni nasan me nake cewa, ina fa tsaye bakin kofar dakin haihuwa daga safe har dare sannan aka haifesa, sai kin ga wahalar da ya ba uwar d'an banxan, ai ko aka haifosa lafcece ya kusa biyun wani jaririn, duk ya cika asibiti da kuka nyaaa ke kina gani kinsan sadauki aka haifo, gashi jajir da shi fari hulll, gashin kansa kuwa ga bak'i ga cika yanda kika san d'an balarabe, ke ki bari kawai, nan dai muka koma gida na wanke sa tass, baki ga uwarsa ba lkcn yar siririya kamar xata karye ba yanxu da ta ci kudin d'a na iya ci ba ta koma kamar buhun masara, kullum zanyi wanka da sassafe daga gidana in tafi gidan Ahmadu yi ma fitsararren yaron nan wanka, don babu abinda uwar ta iya wai tsoron jaririn ma take don bala'i, a haka har yayi wata uku ya koma yanda kika san bredi wato ya xama wani lukeke, ga kyau tsantsa, ba sai uwar tayi ta cika masa nono yayi ta tumbudi ba duk k'arni??" Imaan ta fashe da dariya har da kyakyatawa tace "Shi yayan?" Inna tace "Wllh shi, to ni ko ina xan iya kazanta da k'arni, oh oh nan na taka mata burki, ga uwar kazama dn har sannan tana tashen kuruciya ni fa ko abincin gidan bana iya ci da, ana haka har Mujaheed ya kai shekara biyu, ba sai naga ana neman hallaka yaron ba, ba shi da aiki sai kukan banxa, fitsari a tsaye kashi a tsaye, ga uban shan yogurt, to da yake ba yanda na raini ubansa ba kenan bakina a leko na daukesa, kin ji mafarin komawansa waje na kenan, kuma Mujaheed bai bar gu na ba sai da uban ya biya masa kudin karatun likita a kasashen turai bayan ya gama sakandari, to ace banyi wahala da d'an banxan yaron ba kuwa, tsakaninsa da iyayensa fa sai dai bayan kwana biyu yaje ya gaishesu ya dawo, ko k'uda bana yarda ya ta6a min shi balle shegun kishiyoyina da duk suka mace yanxu, Allah dai ya ji kansu amma shari'ar mu da su sai a lahira...." Imaan tace "Ni lokacin ma ba a haifeni ba koh?" Da mamaki Inna tace "Oh oh kaji wata magana kamar na ta6a66u, wa ke ta ke, ke da aka haifa jiya jiya, a hannuna fa kika fado, ai wannan labarin da nake baki a lkcn mu duk mun dauka uwar ki juya ce...." Imaan ta mike xaune ta hade rai tana kallon inna, inna ta gyara xama tace "An auro uwar Mujaheed da shekara uku fa Ubanki Bukar ya auri bafillatanar uwar ki tana tallan nono a lkcn, a gidan sa fa tayi wnn karatun da take takama da shi" Imaan ta daure fuska tana kallonta, inna tace "Bayan an auri Uwar ki Aisha da yan watanni na tursasa Ahmadu ya sake aure shine fa ya auro Uwarsu isuhu, don a lkcn Rukayya na tashen rashin kunya duk an hure mata kunne, ga kazanta duk ta bi ta ru6ar min da gidan d'a na, To ita kuma uwar isuhu lkcn kawar Mamarki ce, kin ji musabbabin rashin shirin Rukayya da mamanki har yau, Rukayya ta dinga jin haushin Aisha tunda kawarta ta aure mata miji, Uwar su isuhu na shigowa da wata goma sai gashi ta haifo wannan d'an albarkan isuhu shi ma dai a gabana aka haifesa ina tsaye, ke ko uwar ki shiru kamar malam ya ci shirwa, ke in takaice maki har bayan shekaru aru aru sai dai uwar ki ta ci ta sha tayi kashi duk tayi bake bake a gida babu haihuwa babu dalilinsa, babu yanda banyi da Bukar ya karo mata ba amma yaron nan ya bijire min to duk ta shanye min shi ta rarraba min sunansa inda bai kamata ba, ke kinga bafillatani? To wllh kiji tsoronsa mugwaye ne na kin karawa, ni dai na dage rokon Allah ba dare ba rana don Allah ya warware abinda tayi ma d'a na, to wllh karshe sai da Ahmadu yayi 'ya ya shidda sannan uwar ki ta haifo ki, murna gun mahaifinki kuwa ba a cewa komai, duk lkcn fa ba mu san ba lafiyayya bace ke din, nayi ta xuba idon xuwan kanninki amma shiru, astagfirullah wa ya sani ma ko sai a lahira idan ana haihuwar tunda gashi yanxu kin doshi ashirin, kuma tun da kika fara wayo Bukar ya kulla adashin da ba kwasa da asibiti, shine ake nan har yanxu jiya e yau, ni yanxu mai kwasan ki ma nake tausayi wllh kada ya kasa rike ki, wannan idan talaka kika aura ae sai dai mu xo wataran mu dau gawarki muna koke koke, to banda haka sata xai yi ya kai ki asibiti? abinda Bukar yace min a kalla magungunan ki suna yin kusan dubu hamsin duk wata, wa xai iya wannan idan ba mai kudi ba irinsu yaran d'an tata, mu dai Allah ga mu gare ka, ka yaye ma jikata wannan iska da ya sa ta gaba yake cutan ta, ita kenan gun d'a na" Imaan na hararanta tace "Daga labarin yaya kin wani dawo bada labarina kamar an tambayeki, har na gaji da jin labarin nan a gidan nan" inna tace "Toh wa ke ta wani yaya da barin gidan xai yi gaba daya, ai yau sai ya san ya ta6a uwar masu gida" Da sallama Abba ya shigo parlon, Inna ta daure fuska, Daddy ma ya shigo parlon Mujaheed na biye da shi a baya, inna na ganin Mujaheed tace "Ni dai n shiga uku, mutumin nan ya fitar min a parlo don ba ruwana" Mujaheed ya durkusa d'an nesa da ita ya sunkuyar da kansa yace "Kiyi hakuri inna" inna tace "Oh oh Allah, ni dai wllh sai naga kamar tsoron yaron nan ku ke Ahmadu, ni cewa nayi ku taso sa ya bani hakuri? Me xanyi da hakurinsa, idan da amana Mujaheed zae dinga fifita uwarsa a kai na kuwa? Ni da na ci fitsarinsa na ci kashinsa ba irin wahalar da ban yi da shi ba, wannan wani irin fitina ne, me yasa Isuhu baya min haka?" Shi dai Mujaheed bai dago ba, inna tace "Toh ni dai a bar min parlo na" Daddy yyi murmushi bai dai ce komai ba, Abba yace "Mu dai sai dai mu ce kiyi hakuri, shi kuma nasan maganinsa" inna ta wani tsuke fuska bata ce komai, Imaan dai na kwance sai murmushi take, Abba na kallon Mujaheed yace "On a serious note Mujaheed be careful... you had better respect yourself in this house, and mind you no matter how she does her things, how she behaves, how annoying she might be, she is still my motherr, yes she is my mother I can't change her from who she is, and you have got to respect her to the fullest, you keep that grandma and grandchild play aside since she doesn't cherish that, she have got all right to complain of ur mother, let her be entitled to her opinion, today shud be the last that she will complain of ur attitude toward her Muhammad am I clear" Mujaheed bai iya ya dago kansa ba yace "in sha Allah Abba" Daddy yace "Maa sha Allah" inna da sai tabe baki take tace "Oho dai duk a banxa tunda baxa ku iya koransa a gidan ba" Mujaheed yyi kasa da murya yace "Kiyi hakuri" tace "Tashi ka bani waje, ba dai aure xaka yi ba wataran, wllh duk sai matar ta rama min abinda uwarka tayi min a duniyar nan, takanas xan tattara kayana wllh in koma gidanka da xama duk ni xan dinga koya ma yarinyar, nan Rukayya xata ji ko da dadi ko babu" Mujaheed dai bai ce komai ba, Abba yace "Leave now" mikewa yyi yana hararanta ta gefen ido ya fice daga parlon, Imaan ta fara dariya kasa kasa. Ranan juma'ah da daddare Inna na xaune parlonta Imaan kuma na kwance kan kujera gaba daya ta gaji da labarin da inna ke bata, tana son tashi ta wuce amma ciwon da kafarta ke mata yasa ta kasa tashi, tun magrib take wajen bayan ta kawo mata abinci har wajen tara da rabi yanxu, Inna tace "To kin ji abinda ya raba ni da uwar d'an gwate kenan, kuma fa lkcn kakanku bai san ina xuwa ba, kai jama'a na xuba farin jini gun masu kudi wllh" Imaan dai bata tanka ta ba, bude kofar parlon aka yi Mujaheed ya shigo da sallama, Inna tace "Dama shi kadai ne me shigo min da sallama banda su oh oh" Ta gefen ido Imaan ta kalleta, ya ajiye ledan hannunsa yace "Gashi" ta jawo ledan tana budewa tace "Lahh kaza ce kamar yasan ina marmari wllh " Imaan ta mike xaune, inna ta hade rai ta rufe ledan, mikewa Mujaheed yyi ya dauko plate ya ajiye gabanta, ta mayar gefe tace "Ni dai wllh kuna takura ni gidan nan kai da Imaan ba haka isuhu da su maimoona ke min ba, su basu da sa ido" ta hade rai ta bude ledan ta dau cinya daya ta dungura masa a plate din, dariya yyi ya dauka yace "Ni fa na siya maki kazar ba Abba ba" Inna tace "Auuu" kara bude ledan tayi ta fiddo tsoka daya ta manna masa kan plate din, Ta kalli Imaan tace "Naga kina son albasa da kabeji dauko kwanon can da kika ci abinci in kwashe maki in hada maki da tsoka daya" Imaan tace "Ni nace maki xan ci kaza?" Inna tace "Toh na sani? Gani nayi kin xabura kin tashi kamar Bukar ya siyo min" Daga haka ta kai cinya baki tana ci tace "Allah maka albarka Mujaheed duk cikin jikokina kafi jin k'aina wllh, shi sa ma kana aure zan tattara yanawa yanawa in koma gidan ka na rantse" ya xaro ido yace "Gidan wa?" Ta kallesa tana washe baki tace "Gidan ka" yace "A'a wllh ga yar gaban goshin ki nan kice kuma gidana" tace "Waye yar gaban goshi na?" Yace "Gata nan xaune" inna tace "Oh oh ni gidan ka xan xauna xai fi min kwanciyar hankali, idan matar ka xata rainani nasan xajka taka mata burki kai da baka son abinda xai ta6a ni, wannan salubabbiyar kuma ai yunwa ma kadai ya isa ya koro ni, ni fa ban jin imaan ta iya girki tunda take ko tafasasshen ruwan xafinta ban taba d'andanawa ba" dariya Mujaheed yyi, Imaan ta wani hade rai tana kallon inna, Mujaheed yace "Kinga idan tayi aure xaki d'an dana idan kin koma gidan ta da xama" Inna tace "Ni fa baxan xauna gidan imaan ba gidan ka xan xauna wllh" yace "Wllh baxa ki xaunar min gida ba sai dai nata" Inna tace "Toh me yayi xafi haka, wannan satin idan nayi gidan ka wani satin sai inyi a gidan ta duk da nasan a rame dai xan dawo daga gidan nata amma dole naka naka ne, idan na koma gidan ka sai in murmure" Mujaheed yyi dariya yace "Inaaa ba wannan xancen gidan mijinta ko gidan Yusuf xai fi maki kwanciyar hankali amma gida na kam sai dai ki hangesa daga nisa shi ma kuma a photo, Kinga duk sanda mijin nata ya gaji sai ya koro ki da ita" Inna tace "Wai tsaya Mujaheed da kake wannan xancen da kudin asibiti mijin xai ji ko da nawa dawainiyar ka fa san irin cimar da nake ci bana banxa bane, gwara dai a bar sa ya ji da jinyarta, ni kuma in xauna gidan ka ko Yusuf koh Maimoon, amma ina ni ina xaman gidan imaan ga yunwa dai kiri kiri tunda ba girki take ba sai a wani fake da ciwon numfashi kamar yanda uwarta ke cewa" fuu imaan ta mike xata fita cikin rashin sani plate din da ta ci abinci ta bari wajen ya xamar da ita sai ga ta rijib a kasa, wani ihu ta fasa da karfi tana cewa wayyo kafarta, Inna ta xaro ido ta mike da sauri ta bude kofa tace "Ni dai na shiga uku da jaraba, yi maxa fita da ita Mujaheed, fitar min da ita kar ma ace a parlo na ta fadi" Mikewa Mujaheed yayi yana mata wani kallo yace "Baxa ki tashi ba" cikin kuka tace "Wayyo yaya kafana ya rike baxan iya tashi ba" Inna ta gwalo ido tace "Ka ji ko? Mujaheed ka fitar min da ita kada a sani a bakin duniya" Ganin da gaske ta kasa tashi Mujaheed ya daga ta, ta zaro ido tana yarfe hannu tana cewa wayyo kafarta, inna duk ta rude tana ce ma Mujaheed ya fitar da ita, ko fita basu gama yi ba ta tura su gaba daya, ta kulle kofarta tasa makulli tace "Dama kada a kuskura ace a parlo na ta fadi wllh don ba ruwana" Mujaheed ya xabga ma imaan harara yace "Baxa ki tsaya da kyau ba" cikin kuka tace "Wllh ba karya nake ba yaya kafar ya rike min" kalle kallen wajen ya fara yi, can yayi tsaki ya dauketa kamar yar baby ya nufi bangarensu da ita, gam ta rikesa tana rera kuka.🌟⭐ *Imaan*⭐🌟 _By khaleesat Haiydar_✍🏻 7..... Ajiyeta yyi a balcony ta durkushe wajen yace "Baxa ki shiga ciki ba" cikin rawar murya tace "Baxan iya ba ka kira min Ammi" ya kalli kofar parlon sannan ya daga ta yyi knocking, daddy ne ya bude kofar, Mujaheed yyi kasa da kai, daddy yace "Subhanallah me ya faru?" Mujaheed yace "Faduwa tayi parlon inna" daddy bai ce komai ba ya basu hanya, Mujaheed na rike da ita suka shiga parlon, xata kwanta kan kujera Daddy yace "Take her to her room" Mujaheed ya wuce bedroom dinta daddy ya karasa ya bude masu kofar, kan gado ya kwantar da ita, Daddy na kallonta yace "Ina maganin shafan ki?" Kamar xata yi kuka tace "Yana kan dinning table" juyawa daddy yyi ya fita sai gashi ya dawo rike da methylated cream din dake cikin tube, Mujaheed ya amsa yace "Bari in shafa mata daddy" daga haka ya durkusa yana kallon kafar, daddy ya juya ya fita ya rufo masu kofar, cire Hijab din jikinta tayi ta daga rigar baccin jikinta xuwa gwiwa ta marairaice tace "Yaya ka min a hankali plss" ya mata wani kallo xae shafa mata bayan ya matso cream din ta rike hannunsa da sauri tace "Wayyo Ammina" buge hannun yyi ya mike ya turata ta fada kan gadon ya koma ya durkusa ya fara shafa mata cream din tun daga saman gwiwanta har xuwa fararen toes dinta, runtse ido tayi tana yarfe hannu, ya fi minti biyar yana shafa mata daga karshe taji ya daina, a hankali ta bude idonta, taga ya mike yana kokarin rufe tube din, da sauri ta tashi xaune ta bude zip din yar rigar jikinta tace "Yaya saura bayana" xata sauke rigar kamar warce ta tuna abu ta wani xaro ido ta mike tace "ina xuwa" bathroom ta shiga ta dau towel dinta ta sauke rigar jikinta ta cire sannan ta daura towel din ta fito, ta hau saman gado yace "Kee meye haka?" Ta xaro ido tace "Wayyo to ya xanyi ina son ka shafa min a bayana ne, ciwo yake min da daddare" tana fadin haka ta rungume pillow ta sauke towel din, ya second goma yana kallonta, girgixa kai yyi ya bude man ya matso ya hau saman gadon ya shiga shafa mata daga shoulder dinta har xuwa bayanta, ya kusa minti biyar yana hka, can ya leka fuskarta Bayan ya cire hannunsa ya ga idonta a rufe, har ya rufe tube din bata juyo ba bata bude ido ba, duka ya kai mata a kafarta ta mike xaune a firgice tace "Ammi ba bacci fa nake ba" dauke idonsa yyi, ta wani xaro ido tace "Yaya" ya mike ya ajiye tube din gaban mirror ya fita dakin ya kulle mata kofa, daddy na parlor har sannan, yyi masa sae da safe sannan ya fita parlon. Washegari da safe Imaan ta fito sanye da kayan islamiyya ta shiga kitchen sanin Ammi na can, gaida Ammi tayi, Ammi tace "Kin tashi lafiya?" Ta langwabar da kai tace "Bayan Ammi jiya baki shiga kin duba ni ba nasan kuma ba bacci kike ba, faduwa fa nayi a parlorn inna" Ammi tace "Ehh ban shiga ba, ina jin cikin mafarki kika dauko duvet a closet kika rufe jikin ki" Ta xaro ido tana kallon Ammi, sai kuma tayi dariya tace "Ashe ke kika lullube ni" Ammi tace "Ke da kika kwanta zindir" dariya kawai Imaan tayi, Ammi tace "Garin yaya kika fadi jiya" Imaan tace "Plate ne a hanya, shine Inna ta dinga korana wai kar ace a parlonta na fadi, yaya ne fa ya dawo da ni ko tashi bana iyawa, Allah inna ta iya mugunta" Ammi tace "Toh yyi kyau, amma kina kallon agogo dai ko?" Da sauri Imaan ta leka parlor don ganin agogo, cup ta dauka ta koma parlor ta wuce dinning don hada shayi, takwas saura minti biyar ta fita gidan bayan tayi ma Ammi sallama. Tun da ta dawo karfe sha biyu bayan tayi azahar take ta bacci har karfe uku da mintuna, Fitowa parlor tayi don xuba abinci ta ci, ganin jakar Daddy a parlorn ta kalli Ammi dake tattara masa takardunsa tace "Ammi daddy wucewa xai yi?" Ammi tace "Ko xa ki bi sa" shiru tayi lkci daya mood dinta ya canxa, ta dawo kusa da Ammi ta xauna cikin sanyin murya tace "Ammi me yasa mu ma baxa mu koma Abuja gun daddy ba, bana son yana tafiya ya na barin mu" Ammi tayi dariya tace "Toh ai sai ki gaya masa" dai dai nan Daddy ya fito yana waya, ta mike tana kallonsa kamar xata yi kuka, yana gama wayar ya kalleta yana murmushi yace "Ya aka yi mamana" hawaye ya cika idonta tace "Daddy mu ma mu koma Abuja mana, sai kayi ta zama kai kadai" yace "Wataran xa ku koma my dear, kinyi azahar ma kuwa?" a hankali tace "Nayi" yace "Good" tace "Daddy airport xaka je?" Yace "Ehh, flight xan bi" ta marairaice tace "Toh xan raka ka airport plss daddy" Ammi ta jefa mata wani kallo tace "islamiyyar fa?" Ta marairaice tana kallon Ammi, Daddy yace "Ba sai ta shirya ba mu fita gaba daya, idan ya so sai a ajiyeta a makarantar idan sun dawo airport" da sauri Imaan ta shige dakinta don fara shirin islamiyya , da kyar ta ci abinci bayan Ammi ta tilasta sanin bata wani ci abincin ba daxu da ta dawo, ganin daddy ya fita da jakarsa ta kai plate din kitchen da sauri ta fito ta xura hijab din islamiyyarta ta sa safa da takalmi ta dau jakarta xata fita Ammi tace "Ki tafi da jakar laptop din" dawowa tayi ta dau jakar ta fice da sauri ba tare da ta bi ta kan kudin da Ammi ke cewa taje daki ta dauka ba, Mujaheed ne tsaye kusa da motor daddy rike da makullin mota yana jiran dawowansa daga part din inna da yaje sallama, Maimoon ce ta kwalo ma Imaan kira tana tambayarta inda xata, Imaan tace "Ni motar daddy xan bi ku wuce kawai idan kun shirya kar ku jirani" Mujaheed ya hade rai yace "Ina zaki?" tace "Daddyna xan raka airport idan ya so idan muna dawowa sai a ajiye ni a islamiyyar" yana girgixa kai yace "kama gaban ki.... uban wa xai ajiye ki islamiyya ni na maki kama da driver din ki, daina kallona ki bar nan wajen my friend" Hawaye ya fara kawowa idonta ta tsaya tana kallonsa har sannan, strictly yace "Baxa ki daina kallona ki bace min a nan ba?" Juyawa tayi ta nufi sashinsu da sauri, lkci daya ta fashe da kuka, yana ganin haka ya xaro ido yace "Imaan" kin juyowa tayi, ya fara dube duben babban compound din kafin ya bi bayanta da sauri, har ta kusa shiga balcony dinsu ya fixgota ta juyo ta kara fashewa da kukan shagwaba, rikicewa yyi hango daddy da yyi yana tahowa daga part din inna, yace "Toh me nayi maki, kina son kiyi lattin islamiyya ne?" Cikin rawar murya tace "Toh bayan lkci bai yi ba" yana Satan kallon direction din da daddy ke tahowa yace "Toh naji goge idonki mu je" ta turo baki tace "Saboda kaga daddy na koh?"Wani kallo ya dinga mata kafin ya kama hannunta suka koma gun motar, bude back seat tayi ta ajiye laptop dake hannunta ta shiga tana kallonsa ganin irin kallon da yake mata tace "Yaya ka tuna watarana da za mu je gidan Mama fa'ixa abinda ya faru?" Bai tanka ta ba ya dauke kai, sai da daddy ya fara shiga yyi ma Ammi sallama sannan ya fito ya nufo parking space, yana kallon Mujaheed dake tsaye yace "Sorry for keeping you waiting son" murmushi kawai Mujaheed yyi, daddy ya bude back seat ganin Imaan ciki yace "Mamana why not seat at the front" tace "Noo, I am more comfortable here" yace "A'a dawo gaba" Mujaheed yace "Abba tace ta fi son nan ne" Daddy yyi murmushi ya shiga motar shi ma, Mujaheed ya shiga maxaunin driver, mai gadi ya bude masa gate ya ja motar. Sae da suka hau saman titi Daddy yace "Mujaheed pls ku dinga hakuri da grandma dinku, ita haka Allah yayi ta, mu wa enda ta haifa ma muka iya xama da ita balle ku grandchildren, ya kamata kafi kowa sanin halinta tunda ka xauna gunta, kasan abinda take so kasan abinda bata so, plss bana son in ji kun sake samun matsala kaji?" Yana murmushi yace "In sha Allah Abba" Daddy ya kalli Imaan da ta dauke kai yace "Ke kuma kar ki yarda ta kirani tace kin mata wani abu, wllh zan sa6a maki, tsakanin ki da ita respect babu wasan grandma and grandchild tunda bata so, I repeat respect her ynda xa ki respecting Ammin ki" Imaan tace "Ni dama na daina xuwa part dinta.... Kullum sai tace an mata rashin kunya" daddy yace "Don't try dat, you make sure kinje gaisheta everyday, kinsan Allah duk kika yrda ta kirani ta kawo karan ki xan bar duk abinda nake in dawo in ci kaniyar ki" kamar zata yi kuka tace "Toh yaya fa? Ae shima yana mata rashin kunya, Rahma da Ummi ma haka" Ta madubi Mujaheed ya mata wani kallo ta murguda masa baki, daddy yace "Ae duk na ja masu kunne kuma suna jin maganata ke ce dai mai kunnen k'ashi" Imaan ta bata fuska xata yi kuka, the remaining journey to d airport was silent, Imaan dai sai kumbure kumbure take. Suna isa airport din wajen karfe hudu da rabi, suka raka daddy har ciki, daddy na rike da jakarsa yace "Thanks much sai mun yi waya Muhd" Mujaheed ya dukar da kansa yace "Allah ya tsare Abba" Daddy yace "Ameen" yana kallon Imaan dake goge hawayen idonta, murmushi kawai yyi ya mata side hug yace "Sai mun yi waya anjima daughter, na maki transfer ta account din ki" daga haka ya sake ta ya juya ya wuce, Imaan ta fashe da kuka, Mujaheed dai na tsaye har sai da ya tabbatar baya ganin daddy sannan ya kalleta ya hade rai yace "Toh ki bi sa mana" ta gefen ido ta kallesa bata ce komai ba tana kuka, ya ja tsaki ya juya ya fara tafiya, sai da taga yyi nisa ta bi sa da sauri tana goge idonta...A haraban airport din ta tadda Mujaheed suna gaisawa da wata, Imaan ta ja gefe ta tsaya kamar ance ta waiga taga wani tsaye jikin ride dinsa ya rungume hannu yana kallon saitinta ta cikin black glasses dake idonsa, she couldn't tell ko ita yake kallo, ta dai dauke kai da sauri, bayan few seconds ta kara satan kallonsa taga saitin ta yake kallo still, tayi saurin dauke kai, again ta sake kallonsa, cire glass din idonsa yyi yana kallonta da kyau, a hanxarce ta kauda kai tana son tuna ina ta ta6a ganinsa, bata hakura ba ta kara satan kallonsa ganin bai daina kallonta ba ta juya tana kallonsa directly ita ma, murmushi yyi da har sai da dimples dinsa ya lotsa, ya xura hannunsa aljihunsa ya langwabar da kai yana kallonta dai, Mujaheed ya juya yana kallon Imaan bayan sun gama gaisawa da friend dinsa, ya ga sai kallon mutumi kamar ta samu television take, takawa yyi har kusa da ita yace "Do you have any business with him?" Ta turo baki tace "Toh shi ma ai kallona yake" Mujaheed yace "Wuce mu je kar in kwada maki mari" ta gefen ido ta hararesa ta nufi gun motarsa ya bi bayanta, bude front seat tayi ta juya tana kallon mutumin da bai fasa kallonta ba, Mujaheed yace "Wai kina hauka ne" ta turo baki ta shiga cikin motar, tada motar yayi bayan ya shiga suka bar haraban airport din, sun yi nisa sosai kamar ance ta dago kanta ta ga wani waje da ake gashin kaji, ta kallesa da sauri tace "Yaya" kallonta yayi, ta marairaice masa tace "Don Allah ka siya min kaza plss" yace "In siya maki kaza?" Shiru tayi tana kallonsa, yace "To kudi kika bani?" Ta turo baki, bai sake ce mata komai ba, ganin xa su wuce gun masu kajin tace "Wayyoo yaya plss" kara gudun motar yyi ya wuce wajen, kallonsa ta dinga yi kafin ta dauke kanta, ganin hanyar da ya dauka tace "To islamiyyar fa?" Yace "Sai dai in ajiye ki ki ta fi da kafa daga nan, ni ba drivern ki bane" yana shiga anguwarsu yyi parking gidaje uku kafin nasu ba tare da ya kalleta ba yace "Sauka" bude motar tayi ta fice fuuu ta nufi gate dinsu sai da ya ga ta shiga sannan ya karasa da mota gate din mai gadi ya bude ya shigar da motar. Ko kallonsa Imaan da har kota kusa part dinsu bata yi ba har ta shiga parlornsu, Kallonta Ammi ta dinga yi bayan ta shigo parlon tace "Dawowa kika yi baki tafi islamiyyar ba Imaan?" A hankali tace "Yaya ne yaki kai ni" Ammi tace "Ba har dadin fashi kike ba, ki ci gaba" Shiru Imaan tayi bata ce komai ba, Ammi ta wuce daki ta bar ta parlon. Bayan magrib Imaan na kwance parlor tana kallo, Ammi ta kirata daga kitchen, ajiye remote din hannunta tayi ta mike ta wuce kitchen din, Ammi ta nuna mata abincin Inna tace "Ki kai ma inna" Imaan tace "Ammi da xa mu kai Daddy airport fa sai da ya sake min warning a kan xuwa wajen inna" Ammi tace "So?" Ta marairaice tace "Toh ni kar inje in sake mata wani abu ta kira daddy" Ammi tace "Ni xan dinga kai mata abincin kenan" Kamar xata yi kuka tace "Ni wlh Ammi nace fa baxan sake xuwa part dinta ba har abada" Ammi tace "Toh kar ki je ki bar abincin a wajen" Imaan ta dau abincin rai ba dadi ta fita, Yusuf da Ummi na xaune parlorn Imaan ta shiga ta ajiye abincin, tana kallon Yusuf tace "Ina yini ya Yusuf?" Yace "Lafiya lau Imaan yau ba ciwon kafa kenan" Inna ta kallesa da sauri tace "Kaji wata mugun alkaba'i, kai fata kake kafar su yi ta ciwo kenan? Shi kenan ita kuma sae ta k'are a ciwo kamar warce ta kashe d'an mutum, ku dai 'ya yan Ahmadu baku da kirki, ku dinga sa ma bakin ku linzami don Allah" Yusuf yyi dariya yace "Daga tambaya kuma Hajiya inna?" Inna ta sharesa ta jawo wani leda tana kallon Imaan tace "Gashi nan Mujaheed ya kawo maki daxu, sai ki xauna a nan ki bude ki tsamma kowa don kema haka kike da sa ido, ni wllh ban ma ji dadin zuwanki ba tunanina baxa ki xo ba in cinye inyi nak" Imaan ta bude ledan da sauri, kaza ce babba guda daya sai kamshi da turiri yake, Imaan ta saci kallon kofa sannan ta saci kallon Inna dake goge plate din da xa a dibar mata ta fice parlon a dari da sittin, sake baki inna tayi da plate din hannunta, Yusuf ya kyalkyale da dariya, inna tace "Kaji daya daga dalilin da xa ku ji ance ta tashi kafa ya rike gobe saboda mugun halinta, toh meye kuma nama ni fatima? Halin fulanawan kenan fa rowa da mugunta, shi naman da xata d'an yaga ma kowa shine xata kwasa a guje kamar k'arya?" Dariya kawai Yusuf yake, inna da har hawaye ya kawo idonta tace "Don ubanta ta yi kiba kafin gobe idan ta cinye kaza daya, kuma Allah ya isa rai da aka sa min" Yusuf ya mike ya fice parlon yana ta dariya, mikewa inna tayi tana share idonta ta nufi dakinta tana cewa "Me aka yi aka yi nama kuma don Allah, wani irin nama kuma?? wani irin nama ne ban ci ba a rayuwar nan, kuma shima Mujaheed din da gangan ne, ai yasan shegen rowa gareta da na tambayesa na wa sai ce min yayi xata dibar min, babu yanda ban yi kokarin fahimtar da shi kan cewar da kamar wuya fa shegiyar ta dibar min, to ga karshenta nan ta gudu, a dinga abu ba tsoron Allah" Ummi tace "Toh shi me ye ma na siya mata kaza bayan ko gaishe shi bata yi wlh a gidan nan" Inna tace "Ohon masu, kya bar ni budurwa, ni dai Allah ya isa" Ranan litinin sabon driver da Abba ya daukar masu ne ya kai su schl....🌟⭐ *Imaan* ⭐🌟 _By khaleesat Haiydar_✍🏻 8..... Yau Thursday Imaan na dawowa schl bayan tayi wanka ta ci abinci ta fito parlor ta xauna kusa da Ammi dake xaune, ta langwabar da kai tace "Ammi ina son xan je supermarket in siya pad da turarurruka" Ammi ta kalleta tace "Duk uban turarrukan da kika kwaso ranan sun kare kenan Imaan?" Yar dariya tayi tace "A'a ba su kare ba amma sun kai rabi" Ammi tace "Toh sai ki kira babanki bani da kudin da xan baki ki karo turare" Imaan ta bude ido tace "Ya min transfer din 30k ranan da xai tafi ai" Ammi tace "Tohhhh har 30k, lallai kam Allah ya taimaka" dariya Imaan tayi ta mike ta koma daki, Hijab dinta gogagge har kasa ta fiddo ta saka sannan ta dau karamar jakarta ta sa atm card ta feshe jikinta da turare ta fito parlor, ta durkusa kusa da Ammi tace "Toh Ammi ba ni kudin transport don Allah" Ammi tace "Ki duba gaban mirror a daki" tashi tayi ta shiga ta dauko sannan ta dawo parlon, tace "Yauwa Ammi ina son xan biya ta gidansu Mariya, tun Tuesday bata xo schl ba bata da lafiya" Ammi tace "Waye kuma Mariya?" Imaan tace "Lahh wannan da ke xuwa dubani wani lkcn idan bani da lafiya" Ammi tace "Kice min dai gidansu xa ki je ba supermarket ba" Imaan tace "A'a fa Ammi, kawai tunawa nayi, Ban ma san ko xan gane gidan ba fa tunda sau daya muka taba xuwa da Maimoon, idan ban gane ba kawai sai in dawo gida" Ammi tace "Gwara dai ki gane don ki dubota tunda tana yawan xuwa duba ki" Imaan tace "Toh Ammi" daga haka tayi ma Ammi sallama ta fita Ammi na tunatar da ita tayi addu'an fita gida, tana isowa part din su Yusuf taga Umma da wata kawarta xaune a waje kan fararen kujeru, Imaan ta dauke kai duk da sun hada ido har ta wuce su ta nufi gate, Hajiya Salaha tana kallon Umma tace "Wace fitsararriya ce wannan kuma" Wani murmushi Umma tayi tace "Yar wajen Aisha" Hajiya salaha tace "Ikon Allah ita ce ta girma haka?" Tabe baki Umma tayi, Hajiya Salaha tace "Ita Aishar ta sa kar ta gaishe ki gidan nan kenan?" Umma tayi yar dariya tace "Ga dahir kin gani, ai fa ko idona xai makale cikin nata shegiyar baxata gaida ni ba uwar ta hanata" Hajiya Salaha tace "Tabdi ita wannan yar ficicciyar yar?" Umma tace "Ba shine bayan na dawo gidan nan naga ita da Mujaheed da bai san ciwon kansa ba bai san ciwon mahaifiyarsa ba tamkar su yi 6ude, ya maida Aisha kanwar uwarsa bashi da tamkar ta gidan, ita kuma yar mai ciwo yau mai ciwo gobe tunda sickler ce idan kin ga abinda yake mata ko kanninsa su Ummi bai masu, in takaice maki duk dai Aisha ta bi ta shanye min shi yanda ta shanye kanin ubansa, yanda kika san xai mata sujjada" Hajiya Salaha tace "Ikon Allah" Umma tace "Ae tuni na tashi tsaye, nice can nice nan, da taimkon Allah da taimakon Magajiya na kwato d'a na da karfi da yaji, yanxu ko ga maciji basa yi a gidan bangaren ma ya daina xuwa, I can't risk that, uban waye bai san tsafi Aisha take ba, gashi dai ta hana kanin babansa karo matar da xata haifo masa 'ya yansa duniya ta rufe masa baki ta hada sa da 'ya sickler kullum ana hanyar asibiti ana kashe Dan banxan kudade, Allah kenan, kuma in dai ina numfashi a haka yarinyar nan xata kare yau lafiya gobe babu, in Allah ya yarda sai yar nan sai ta xame masu jaraba duk sai ta tsiyace su muna nan muna gani, kee duk wanda xata ra6a ma wllh sai ya tsiyace, haka nan kuma xata yi ta xama ba mashinshini.... to ubanwa xai iya da ita ta kassara tattalin arxikinsa, ni fa duk duniya billahil azim bani da makiyiya da ya wuce Aisha, wllh xan iya yin komai don in toxarta ta da yarta, ni ko kishiyata ban jinta yanda nake jin Aisha, kuma yanda tasa aka toxarta ni aka min kishiya sai na toxarta ta ita ma ko ba jima ko ba dade, ina nan dai kan bakana lokaci kawai nake jira" Hajiya Salaha tace "Ae ko kar ki yarda wllh, ki mata fiye da wanda ta maki ma" Umma tace "Yanxu gobe ma akwai inda xa ni tare da magajiya da sai ki fito mu je tare, wani take take na fara gani nake son taka ma abun burki tun wuri" Hajiya Salaha tace "Haba na me kuma?" Umma tace "Ki ji fa don walakanci yanxu sai su yi ta makala ma Mujaheed ita ya kai ta asibiti, ga uban kudaden da xai kashe wanda nasan ko ance xa a basa baxai amsa ba to akan wani dalili? Shi ya dauro mata ciwon? Na samu na rabasa da shegiyar yarinyar suna kara lika masa ita to gwara in kara xage damtse, ba wani ke nemo masa kudin ba kuma kudinsa ba na banxa bane, su je can su da suka haifeta su karata da cutan ta" Hajiya Salaha tace "Gaskiya kam Allah ya kai mu goben idan kin fito ki kirani" Tunda Imaan ta fito Yusuf dake xaune tare da mai gadi da sabon drivernsu ke kallonta, yyi murmushi yace "Ina xuwa Imaan din daddy?" Rufe fuska tayi tace "Shopping mana" Ya wara ido yace "Kaji Hajiya Imaan, in taso mu je ki min shopping din nima" dariya tayi ta make kafada tace "mu je dai ka biya min" yyi murmushi yace "abun yar haka ne kenan, to wa xai kai ki?" Ta buda hannu tace "Napep xan shiga" ya bude ido yace "Salon ki kwaso k'ura ki dawo mana da asthma?" Turo baki tayi yace "A'a bari driver ya kai ki ya dawo dake kawai" Ta wara ido tace "Da na ji dadi" Ya kalli sabon drivern dake murmushi yace "Toh driver xa a ajiye mana ita a supermarket" ya mike yace "In sha Allah, bari in fiddo motar" daga haka ya shiga cikin compound din, Sai a sannan Imaan ta ga Mujaheed dake xaune kan farin kujera nesa da su yana danna wayarsa, tana kallonsa ya jefa mata wani harara, ta turo baki ta dawo kusa da Yusuf tace "Ya Yusuf jiya da na fita inna ta debar maka dambun koh?" Dariya yyi yace "Aa bata ban ba" ta tabe baki tace "Ba wani nan nasan dama jira take in tafi sai ta xuba maka ita ma ta ci, ni da ba ma cin dambu nake sosai ba" yace "Ae ko sai kin ji dadin da dambun yyi, cewa tayi ita ma ta rama abinda kika mata" bata fuska tayi tace "Ai nasan sae ta baka nice dai baxata ba" Driver na shiga compound din ya gaida su Hajiya da ladabi yana rike da makullin motar ba ta amsa gaisuwar ba tace "Ina xaka?" Yayi kasa da kai yace "Hajiya karama xa a ajiye a supermarket" Umma na masa wani kallo tace "Anya kasan wanda ya dauke ka aiki gidan nan kuwa?" Shiru yyi yana kallonta, tace "Toh ita warcan da kake gani ubanta daban a gidan nan, kuma ba shi ya dauke ka aiki ba, mai nan bangaren ne ke biyanka don haka ka maida hankalin ka, ka wuce ka ban wuri nan da 'yan mintuna xaka ajiye kawata gida" kansa a kasa ya risina yace "Ayi hakuri Hajiya ban sani bane" tace "Ehh ka sani yanxu ai" hakuri ya kara bata ya juya ya fita compound din, Yusuf na kallonsa yace "Ya aka yi?" Yayi kasa da kai yace "Hajiya ce tace xa a ajiye bakuwarta yanxu" Tsaki Yusuf yyi ya mike Mujaheed ya daga kai yana kallonsa, Yusuf na kallon Imaan yace "jira in dauko mota in ajiye ki" a hankali tace "Toh nagode" banda hararansa babu abinda Hajiya take don tasan shi xai sa driver ya fita da imaan, ta ja tsaki bayan ya fita da motarsa waje, Imaan ta bude front seat ta shiga ya bar layin, sai bayan sun hau saman titi yace "Amma dai baxa ki shanya ni a mota idan kin shiga shopping din ba" yar dariya tayi tace "Kasan me ya Yusuf kawai idan ka kai ni ka wuce ba gida xan dawo ba" Yace "Ina xa ki?" Tace "Xanje duba kawata bata da lafiya" yace "Wani anguwa?" Ta fada masa tana kallonsa yace "Su Imaan an fara hankali xa a je duba Mara lafiya" dariya ta fara yi, har suka isa Supermarket din Yusuf na tsokanarta, Bayan yyi parking yace "Kar ki shanya ni Imaan, in har kika dde to baxa ki same ni nan ba, ga ATM dina kiyi amfani da shi ai kinsan pin din" tace "Ya Yusuf ka wuce kawai ba gida fa xan koma ba nace, kuma Daddy ya turo min kudin shopping din" yace "Anya gidan kawarki kadai xaki je kuwa Imaan" ta turo baki tana kallonsa, yyi murmushi yace "Toh yi hakuri, napep xaki hau xuwa gidan kenan?" Ta gyada masa kai yace "In ji kin fito da nose mask din ki?" Tace "Ehh yana jaka" yace "Toh kar dai ki jima gidan kawar don ni baxan iya ba ammi hakuri ba" tayi dariya tace "Sae ka bata ni dai idan xata dokeni" dubu daya ya mika mata yace "Sai ki hau napep din tunda Daddy ya baki kudin shopping" ta amsa tace "Nagode" daga haka ta daga masa hannu ta nufi entrance din supermarket din. Tun a bakin entrance din yake kallonta har ta shiga mall din yana biye da ita a baya, gun turarurruka ta nufa, bayan ta dau wa enda take so har shidda, ta tafi gun pad, ta duka ta dau pad manya biyu kenan sai gashi yana xuwa toward her, suna hada ido gabanta yyi mugun faduwa don rass ta ganesa, da sauri ta ajiye pads din hannunta ta dau dettol dake wajen guda biyu, har ya iso kusa da ita kallonta yake daga cikin bakin spec dake idonsa, ta dauke kai ta dau wani sabulun ma ta sa a basket din hannunta xata wuxe, yace "Assalamu alaikum" ba tare da ta kallesa ba ta amsa, yace "Good evening" Tace "Same" yace "Kin gane ni kuwa?" Kallonsa tayi bata ce komai ba tayi saurin sunkuyar da kanta ta shiga jera kayan basket din hannunta, yyi murmushi yana kallonta yace "Dama saboda kina tare da yayanki ne kika kafe ni da ido jiya a airport, yanxu kuma gashi kin kasa" juyawa tayi xata wuce yace "Wait" juyowa ta kuma yi, ya duka ya dau pads din da ta ajiye ya sa mata cikin basket din, still tayi a tsaye, ya wuce shi kuma gun counter, turo baki tayi ta bi sa da kallo ta gefen ido, bayan wasu sakwanni ta bi bayansa, bata yadda ta tsaya gun da xai biya nasa kudin wines din da ya siya ba a mall din, duk da mutanen da suka fi yawa a next counter din can ta tafi ta tsaya, ana xuwa kanta ta bude jaka xata fiddo atm card dinta taga ya mika masu nasa, juyawa tayi tana kallonsa ya saka masu pin dinsa a pos din, imaan dai ta kasa cewa komai, suka cire kudinsu suka mayar masa card dinsa ya nufi kofar fita, ledan kayanta ta amsa bayan an mata packaging, gabanta ya dinga faduwa har ta fita bata fatan ganinsa a waje, ai ko tsaye ta gansa jikin ride dinsa, da sauri ta dauke kai ta nufi bakin titi, ya bi bayanta har ya isa Inda take yace "In ji yau yaya bai ce ki taho shopping da kafa ba" bata ce komai ba kuma bata kallesa ba, yyi murmushi yace "Toh muje in ajiye ki a gida?" Kamar jira take tace "Nooo" daga haka ta tsayar da adaidaita fuskarta daure ta shiga, mai napep na tambayarta inda xata je tace "Mu je gaba" bin su yyi da kallo yana murmushi, sai bayan da suka yi nisa Imaan ta fada ma mai adaidaitan anguwar da xa ta. Suna isa ta kasa gane gidan, mai napep din yace "Toh kiyi tambaya mana" a hankali tace "To wa enda ban sani ba xan tambaya? Kamar fa wancan layin ne" ya juya yana kallonta yace "Duk fa kin sa na xagaye anguwar nan" Shiru tayi tana kallon layin da suke tsaye ciki banda haushin karnuka baka jin komai ko ina silent" mai napep din yace "Duk na kona mai na" yana fadin haka ya sakko don samun wanda xai ma tambaya duk da ba kowa silent layin sai mota daya dake tahowa, kana ganin layin kasan na manyan mutane ne sosai, ya kalleta yace "Ya kika ce sunan layin?" Fada masa tayi, mai motar na isowa inda suke ya tsaya ta dalilin tsaida shi da mai adai daitan yayi, Ya sauke glass mai adai daitan ya kalleta yace "Ya layin ma?" Ta hade rai don ta gaji da gaya masa sunan layin ta sakko daga napep din tana sake nanata masa, shiru tayi tana kallon mai motan kamar yanda shi ma ke kallonta, ya d'an yi murmushi yace "Ashe anguwar mu xa ki xo dama" bata ce komai ba ta wani hade rai, yace "Gidansu wa kike nema?" Ta sauke kanta kasa tace "Mariya Ahmad" Yace "I think wancan gidan ne" ya nuna mata gate din gidan, sae a sannan ta gane wajen, ta kallesa da kyar tace "Nagode" daga haka ta ciro dubu daya ta mika ma mai adai daitan ya bata dari biyar ta wuce xuwa gate din. Sosai Mariya taji ddin ganin Imaan ta rungumeta tace "Imaan a gidanmu, lallai yau za ayi ruwa da kankara, taya kika gane nan" imaan tayi murmushi tace "i just came to check on ur health daga shopping mall nake" Mariya tace "wllh naji sauki sosai, gobe in sha Allah xan je schl" Imaan tace "Toh Allah ya kara lafiya" Mariya zata dauko mata drinks a fridge tace "Aa ni fa baxan sha ba bana shan abu mai sanyi" Mariya tace "Ehh akwai mara sanyi ai" murmushi kawai imaan tayi Mariya ta tafi dauko mata mara sanyi, sosai Mariya ke son Imaan sai dai Imaan bata da saurin sabo kuma bata sakewa da mutane duk da kowa yasan mahaifin Mariya mai kudi ne sosai kuma sananne, har kawance ake son yi da ita, yawanci Mariyar ce ke xuwa gidansu Imaan dubata idan ta kwana biyu bata je schl ba, ita ko Imaan tun da suka je gidansu Mariyan duba yayarta da aka ma aiki tare da classmates dinsu bata sake komawa gidan ba sai yanxu, bayan boko islamiyyarsu ma daya kuma Mariya ma na da haxaka both schl da islamiyya tamkar Imaan din, Duk yanda imaan ta so tafiya Mariya ta ki yarda wai sai mamarta ta dawo sun gaisa, mahaifiyarta na dawowa kuwa ta kai Imaan har parlonta, Imaan ta duka kasa ta gaisheta da fara, matar mai kirki ta tarbe ta tana tambayarta mamarta, Imaan tayi murmushi tace "Tana gida" Aunty tace "Ya karatun fa" imaan tace "Alhmdllh" Aunty tace "Maa sha Allah sai ku yi ta dagewa, Allah ya bada sa'a kin ji" bude kofar dakin aka yi duk suka kalli kofar, xaro ido Imaan tayi tana kallonsa gabanta na faduwa, ya mata kallo daya kafin yace komai Aunty tace "Har ka dawo Sadeeq" yace "Ehh na dawo, ina yini" tace "Lafiya lau" Mariya tace "ina yini ya Sadeeq" yace "Lafiya lau" Imaan ta sunkuyar da kanta, yana kallon Mariya yace "Bakuwa kika yi" Mariya tace "Eh yaya, classmate dita ce Imaan" Yace "Oh I see, sannu da xuwa bakuwa...." Imaan ta kasa dago kanta tace "Ina yini" yace "Lafiya lau" Daga haka ya juya ya fita, Imaan na kallon Mariya tace "Xan tafi Mariya" Turaren Humra mai yawa Aunty ta dibar ma Imaan da smart collections, Mariya ta amsar mata tana godiya, Imaan tayi mata godiya ta mike suka fita tare da Mariya Aunty na cewa ta gaida ummanta, Bedroom din Mariya Imaan ta shiga daukan jakarta da ledan shopping dinta, bayan ta dauka tana facing Mariya tace "Waye wannan da ya shigo Mariya?" Mariya tace "Wai ya Sadeeq? Yayana ne shi" Imaan ta xaro ido da sauri tace "Da gaske?" Mariya tace "Kin san sa ne?" Da sauri Imaan ta girgixa kai tace "A'a tambaya kawai nake" Mariya tace "He is my stepbrother, ga bangarensu can, kina shigowa compound part dinsu xa ki fara gani" Imaan tace "Ayya, ni dai xan wuce kar Ammi ta fara kirana" daga haka ta fita Mariya na biye da ita, a parlor suka tadda Aunty da Sadeeq, da fillanci Mama ke ce ma Sadeeq tunda fita xai yi ya daure ya ajiye Imaan ko bai kai ta har gida ba, Imaan tayi murmushi tace "Aunty ya bar shi xan hau napep" Mariya ta fashe da dariya, Aunty tayi murmushi tace "Ashe dai kina ji, kin bar kawar ki a baya, ba abinda ta iya sai shashanci" Imaan ta kalli Mariya da ta cinno baki tana murmushi, Sadeeq ya mike yace "Toh bari in ajiye ta" Imaan ta d'an xaro ido, Babu yanda ta iya, bata kuma yi ma mahaifiyar Mariya musu ba, suka fita tare da Mariya dake rike da ledan ta bayan Sadeeq ya fita parlorn, Aunty ta bi su har bakin kofa tana ce mata ta gaida ummanta, cikin motar suka tadda Sadeeq, Mariya ta bude mata front seat Imaan ta sunkuyar da kanta ta shiga ba don ta so ba, Mariya tace "Byee Friend sai mun hadu schl gobe, nagode sosai" murmushin karfin hali Imaan ta mata bata ce komai ba, Mariya na kallon Sadeeq da ya tada mota tace "Ya Siddiq drive my friend carefully fa" wani kallo yyi mata bai dai ce komai ba yyi horn, Mariya ta koma ciki tana dariya, har suka hau saman titi babu wanda yace komai cikinsu, bayan wani lkci yace "Wani anguwar xa ki?" Tana wasa da fingers din ta tace "Malali" bai ce komai ba, sai da suka kusa bayan kusan minti sha biyar sannan yace "Wani layin?" Ta gaya masa, daga nan kuma ta dinga nuna masa Inda xai bi har suka shigo gate din layinsu, dai dai gidan ta nuna masa yayi parking ya juya yana kallonta, bata yarda ta kallesa ba tana daukan ledanta dake kan kafarta tace "Nagode" yace "Welcm" daga haka ta bude motar ta fita ta rufe masa motarsa ya bi ta da kallo, Tsaye taga Mujaheed bakin gate da alamar fita xai yi don makullin motarsa na hannunsa, ya kalleta ya kalli motar ya sake kallonta da wani expression, ta wani daure fuska duk da faduwan da gabanta ke yi abinda yayi ma Maimoon ranan don an ajiye ta a mota ya fado mata a rai, turo baki tayi ganin ya ki matsawa daga gate din sai kallonta yake, ta raba ta gefen sa har tana bugesa ta shige gidan da sauri, juyowa yyi yana ci gaba da kallonta, tana ganin haka ta kwasa a guje xuwa part dinsu, sai da ta isa entrance din parlonsu ta tsaya ta juya tana kallonsa, har sannan kallonta yake, ta turo baki ta bude kofa ta shige ta kulle. 🌟⭐ *Imaan* ⭐🌟 _By khaleesat Haiydar_✍🏻 8..... Yau Thursday Imaan na dawowa schl bayan tayi wanka ta ci abinci ta fito parlor ta xauna kusa da Ammi dake xaune, ta langwabar da kai tace "Ammi ina son xan je supermarket in siya pad da turarurruka" Ammi ta kalleta tace "Duk uban turarrukan da kika kwaso ranan sun kare kenan Imaan?" Yar dariya tayi tace "A'a ba su kare ba amma sun kai rabi" Ammi tace "Toh sai ki kira babanki bani da kudin da xan baki ki karo turare" Imaan ta bude ido tace "Ya min transfer din 30k ranan da xai tafi ai" Ammi tace "Tohhhh har 30k, lallai kam Allah ya taimaka" dariya Imaan tayi ta mike ta koma daki, Hijab dinta gogagge har kasa ta fiddo ta saka sannan ta dau karamar jakarta ta sa atm card ta feshe jikinta da turare ta fito parlor, ta durkusa kusa da Ammi tace "Toh Ammi ba ni kudin transport don Allah" Ammi tace "Ki duba gaban mirror a daki" tashi tayi ta shiga ta dauko sannan ta dawo parlon, tace "Yauwa Ammi ina son xan biya ta gidansu Mariya, tun Tuesday bata xo schl ba bata da lafiya" Ammi tace "Waye kuma Mariya?" Imaan tace "Lahh wannan da ke xuwa dubani wani lkcn idan bani da lafiya" Ammi tace "Kice min dai gidansu xa ki je ba supermarket ba" Imaan tace "A'a fa Ammi, kawai tunawa nayi, Ban ma san ko xan gane gidan ba fa tunda sau daya muka taba xuwa da Maimoon, idan ban gane ba kawai sai in dawo gida" Ammi tace "Gwara dai ki gane don ki dubota tunda tana yawan xuwa duba ki" Imaan tace "Toh Ammi" daga haka tayi ma Ammi sallama ta fita Ammi na tunatar da ita tayi addu'an fita gida, tana isowa part din su Yusuf taga Umma da wata kawarta xaune a waje kan fararen kujeru, Imaan ta dauke kai duk da sun hada ido har ta wuce su ta nufi gate, Hajiya Salaha tana kallon Umma tace "Wace fitsararriya ce wannan kuma" Wani murmushi Umma tayi tace "Yar wajen Aisha" Hajiya salaha tace "Ikon Allah ita ce ta girma haka?" Tabe baki Umma tayi, Hajiya Salaha tace "Ita Aishar ta sa kar ta gaishe ki gidan nan kenan?" Umma tayi yar dariya tace "Ga dahir kin gani, ai fa ko idona xai makale cikin nata shegiyar baxata gaida ni ba uwar ta hanata" Hajiya Salaha tace "Tabdi ita wannan yar ficicciyar yar?" Umma tace "Ba shine bayan na dawo gidan nan naga ita da Mujaheed da bai san ciwon kansa ba bai san ciwon mahaifiyarsa ba tamkar su yi 6ude, ya maida Aisha kanwar uwarsa bashi da tamkar ta gidan, ita kuma yar mai ciwo yau mai ciwo gobe tunda sickler ce idan kin ga abinda yake mata ko kanninsa su Ummi bai masu, in takaice maki duk dai Aisha ta bi ta shanye min shi yanda ta shanye kanin ubansa, yanda kika san xai mata sujjada" Hajiya Salaha tace "Ikon Allah" Umma tace "Ae tuni na tashi tsaye, nice can nice nan, da taimkon Allah da taimakon Magajiya na kwato d'a na da karfi da yaji, yanxu ko ga maciji basa yi a gidan bangaren ma ya daina xuwa, I can't risk that, uban waye bai san tsafi Aisha take ba, gashi dai ta hana kanin babansa karo matar da xata haifo masa 'ya yansa duniya ta rufe masa baki ta hada sa da 'ya sickler kullum ana hanyar asibiti ana kashe Dan banxan kudade, Allah kenan, kuma in dai ina numfashi a haka yarinyar nan xata kare yau lafiya gobe babu, in Allah ya yarda sai yar nan sai ta xame masu jaraba duk sai ta tsiyace su muna nan muna gani, kee duk wanda xata ra6a ma wllh sai ya tsiyace, haka nan kuma xata yi ta xama ba mashinshini.... to ubanwa xai iya da ita ta kassara tattalin arxikinsa, ni fa duk duniya billahil azim bani da makiyiya da ya wuce Aisha, wllh xan iya yin komai don in toxarta ta da yarta, ni ko kishiyata ban jinta yanda nake jin Aisha, kuma yanda tasa aka toxarta ni aka min kishiya sai na toxarta ta ita ma ko ba jima ko ba dade, ina nan dai kan bakana lokaci kawai nake jira" Hajiya Salaha tace "Ae ko kar ki yarda wllh, ki mata fiye da wanda ta maki ma" Umma tace "Yanxu gobe ma akwai inda xa ni tare da magajiya da sai ki fito mu je tare, wani take take na fara gani nake son taka ma abun burki tun wuri" Hajiya Salaha tace "Haba na me kuma?" Umma tace "Ki ji fa don walakanci yanxu sai su yi ta makala ma Mujaheed ita ya kai ta asibiti, ga uban kudaden da xai kashe wanda nasan ko ance xa a basa baxai amsa ba to akan wani dalili? Shi ya dauro mata ciwon? Na samu na rabasa da shegiyar yarinyar suna kara lika masa ita to gwara in kara xage damtse, ba wani ke nemo masa kudin ba kuma kudinsa ba na banxa bane, su je can su da suka haifeta su karata da cutan ta" Hajiya Salaha tace "Gaskiya kam Allah ya kai mu goben idan kin fito ki kirani" Tunda Imaan ta fito Yusuf dake xaune tare da mai gadi da sabon drivernsu ke kallonta, yyi murmushi yace "Ina xuwa Imaan din daddy?" Rufe fuska tayi tace "Shopping mana" Ya wara ido yace "Kaji Hajiya Imaan, in taso mu je ki min shopping din nima" dariya tayi ta make kafada tace "mu je dai ka biya min" yyi murmushi yace "abun yar haka ne kenan, to wa xai kai ki?" Ta buda hannu tace "Napep xan shiga" ya bude ido yace "Salon ki kwaso k'ura ki dawo mana da asthma?" Turo baki tayi yace "A'a bari driver ya kai ki ya dawo dake kawai" Ta wara ido tace "Da na ji dadi" Ya kalli sabon drivern dake murmushi yace "Toh driver xa a ajiye mana ita a supermarket" ya mike yace "In sha Allah, bari in fiddo motar" daga haka ya shiga cikin compound din, Sai a sannan Imaan ta ga Mujaheed dake xaune kan farin kujera nesa da su yana danna wayarsa, tana kallonsa ya jefa mata wani harara, ta turo baki ta dawo kusa da Yusuf tace "Ya Yusuf jiya da na fita inna ta debar maka dambun koh?" Dariya yyi yace "Aa bata ban ba" ta tabe baki tace "Ba wani nan nasan dama jira take in tafi sai ta xuba maka ita ma ta ci, ni da ba ma cin dambu nake sosai ba" yace "Ae ko sai kin ji dadin da dambun yyi, cewa tayi ita ma ta rama abinda kika mata" bata fuska tayi tace "Ai nasan sae ta baka nice dai baxata ba" Driver na shiga compound din ya gaida su Hajiya da ladabi yana rike da makullin motar ba ta amsa gaisuwar ba tace "Ina xaka?" Yayi kasa da kai yace "Hajiya karama xa a ajiye a supermarket" Umma na masa wani kallo tace "Anya kasan wanda ya dauke ka aiki gidan nan kuwa?" Shiru yyi yana kallonta, tace "Toh ita warcan da kake gani ubanta daban a gidan nan, kuma ba shi ya dauke ka aiki ba, mai nan bangaren ne ke biyanka don haka ka maida hankalin ka, ka wuce ka ban wuri nan da 'yan mintuna xaka ajiye kawata gida" kansa a kasa ya risina yace "Ayi hakuri Hajiya ban sani bane" tace "Ehh ka sani yanxu ai" hakuri ya kara bata ya juya ya fita compound din, Yusuf na kallonsa yace "Ya aka yi?" Yayi kasa da kai yace "Hajiya ce tace xa a ajiye bakuwarta yanxu" Tsaki Yusuf yyi ya mike Mujaheed ya daga kai yana kallonsa, Yusuf na kallon Imaan yace "jira in dauko mota in ajiye ki" a hankali tace "Toh nagode" banda hararansa babu abinda Hajiya take don tasan shi xai sa driver ya fita da imaan, ta ja tsaki bayan ya fita da motarsa waje, Imaan ta bude front seat ta shiga ya bar layin, sai bayan sun hau saman titi yace "Amma dai baxa ki shanya ni a mota idan kin shiga shopping din ba" yar dariya tayi tace "Kasan me ya Yusuf kawai idan ka kai ni ka wuce ba gida xan dawo ba" Yace "Ina xa ki?" Tace "Xanje duba kawata bata da lafiya" yace "Wani anguwa?" Ta fada masa tana kallonsa yace "Su Imaan an fara hankali xa a je duba Mara lafiya" dariya ta fara yi, har suka isa Supermarket din Yusuf na tsokanarta, Bayan yyi parking yace "Kar ki shanya ni Imaan, in har kika dde to baxa ki same ni nan ba, ga ATM dina kiyi amfani da shi ai kinsan pin din" tace "Ya Yusuf ka wuce kawai ba gida fa xan koma ba nace, kuma Daddy ya turo min kudin shopping din" yace "Anya gidan kawarki kadai xaki je kuwa Imaan" ta turo baki tana kallonsa, yyi murmushi yace "Toh yi hakuri, napep xaki hau xuwa gidan kenan?" Ta gyada masa kai yace "In ji kin fito da nose mask din ki?" Tace "Ehh yana jaka" yace "Toh kar dai ki jima gidan kawar don ni baxan iya ba ammi hakuri ba" tayi dariya tace "Sae ka bata ni dai idan xata dokeni" dubu daya ya mika mata yace "Sai ki hau napep din tunda Daddy ya baki kudin shopping" ta amsa tace "Nagode" daga haka ta daga masa hannu ta nufi entrance din supermarket din. Tun a bakin entrance din yake kallonta har ta shiga mall din yana biye da ita a baya, gun turarurruka ta nufa, bayan ta dau wa enda take so har shidda, ta tafi gun pad, ta duka ta dau pad manya biyu kenan sai gashi yana xuwa toward her, suna hada ido gabanta yyi mugun faduwa don rass ta ganesa, da sauri ta ajiye pads din hannunta ta dau dettol dake wajen guda biyu, har ya iso kusa da ita kallonta yake daga cikin bakin spec dake idonsa, ta dauke kai ta dau wani sabulun ma ta sa a basket din hannunta xata wuxe, yace "Assalamu alaikum" ba tare da ta kallesa ba ta amsa, yace "Good evening" Tace "Same" yace "Kin gane ni kuwa?" Kallonsa tayi bata ce komai ba tayi saurin sunkuyar da kanta ta shiga jera kayan basket din hannunta, yyi murmushi yana kallonta yace "Dama saboda kina tare da yayanki ne kika kafe ni da ido jiya a airport, yanxu kuma gashi kin kasa" juyawa tayi xata wuce yace "Wait" juyowa ta kuma yi, ya duka ya dau pads din da ta ajiye ya sa mata cikin basket din, still tayi a tsaye, ya wuce shi kuma gun counter, turo baki tayi ta bi sa da kallo ta gefen ido, bayan wasu sakwanni ta bi bayansa, bata yadda ta tsaya gun da xai biya nasa kudin wines din da ya siya ba a mall din, duk da mutanen da suka fi yawa a next counter din can ta tafi ta tsaya, ana xuwa kanta ta bude jaka xata fiddo atm card dinta taga ya mika masu nasa, juyawa tayi tana kallonsa ya saka masu pin dinsa a pos din, imaan dai ta kasa cewa komai, suka cire kudinsu suka mayar masa card dinsa ya nufi kofar fita, ledan kayanta ta amsa bayan an mata packaging, gabanta ya dinga faduwa har ta fita bata fatan ganinsa a waje, ai ko tsaye ta gansa jikin ride dinsa, da sauri ta dauke kai ta nufi bakin titi, ya bi bayanta har ya isa Inda take yace "In ji yau yaya bai ce ki taho shopping da kafa ba" bata ce komai ba kuma bata kallesa ba, yyi murmushi yace "Toh muje in ajiye ki a gida?" Kamar jira take tace "Nooo" daga haka ta tsayar da adaidaita fuskarta daure ta shiga, mai napep na tambayarta inda xata je tace "Mu je gaba" bin su yyi da kallo yana murmushi, sai bayan da suka yi nisa Imaan ta fada ma mai adaidaitan anguwar da xa ta. Suna isa ta kasa gane gidan, mai napep din yace "Toh kiyi tambaya mana" a hankali tace "To wa enda ban sani ba xan tambaya? Kamar fa wancan layin ne" ya juya yana kallonta yace "Duk fa kin sa na xagaye anguwar nan" Shiru tayi tana kallon layin da suke tsaye ciki banda haushin karnuka baka jin komai ko ina silent" mai napep din yace "Duk na kona mai na" yana fadin haka ya sakko don samun wanda xai ma tambaya duk da ba kowa silent layin sai mota daya dake tahowa, kana ganin layin kasan na manyan mutane ne sosai, ya kalleta yace "Ya kika ce sunan layin?" Fada masa tayi, mai motar na isowa inda suke ya tsaya ta dalilin tsaida shi da mai adai daitan yayi, Ya sauke glass mai adai daitan ya kalleta yace "Ya layin ma?" Ta hade rai don ta gaji da gaya masa sunan layin ta sakko daga napep din tana sake nanata masa, shiru tayi tana kallon mai motan kamar yanda shi ma ke kallonta, ya d'an yi murmushi yace "Ashe anguwar mu xa ki xo dama" bata ce komai ba ta wani hade rai, yace "Gidansu wa kike nema?" Ta sauke kanta kasa tace "Mariya Ahmad" Yace "I think wancan gidan ne" ya nuna mata gate din gidan, sae a sannan ta gane wajen, ta kallesa da kyar tace "Nagode" daga haka ta ciro dubu daya ta mika ma mai adai daitan ya bata dari biyar ta wuce xuwa gate din. Sosai Mariya taji ddin ganin Imaan ta rungumeta tace "Imaan a gidanmu, lallai yau za ayi ruwa da kankara, taya kika gane nan" imaan tayi murmushi tace "i just came to check on ur health daga shopping mall nake" Mariya tace "wllh naji sauki sosai, gobe in sha Allah xan je schl" Imaan tace "Toh Allah ya kara lafiya" Mariya zata dauko mata drinks a fridge tace "Aa ni fa baxan sha ba bana shan abu mai sanyi" Mariya tace "Ehh akwai mara sanyi ai" murmushi kawai imaan tayi Mariya ta tafi dauko mata mara sanyi, sosai Mariya ke son Imaan sai dai Imaan bata da saurin sabo kuma bata sakewa da mutane duk da kowa yasan mahaifin Mariya mai kudi ne sosai kuma sananne, har kawance ake son yi da ita, yawanci Mariyar ce ke xuwa gidansu Imaan dubata idan ta kwana biyu bata je schl ba, ita ko Imaan tun da suka je gidansu Mariyan duba yayarta da aka ma aiki tare da classmates dinsu bata sake komawa gidan ba sai yanxu, bayan boko islamiyyarsu ma daya kuma Mariya ma na da haxaka both schl da islamiyya tamkar Imaan din, Duk yanda imaan ta so tafiya Mariya ta ki yarda wai sai mamarta ta dawo sun gaisa, mahaifiyarta na dawowa kuwa ta kai Imaan har parlonta, Imaan ta duka kasa ta gaisheta da fara, matar mai kirki ta tarbe ta tana tambayarta mamarta, Imaan tayi murmushi tace "Tana gida" Aunty tace "Ya karatun fa" imaan tace "Alhmdllh" Aunty tace "Maa sha Allah sai ku yi ta dagewa, Allah ya bada sa'a kin ji" bude kofar dakin aka yi duk suka kalli kofar, xaro ido Imaan tayi tana kallonsa gabanta na faduwa, ya mata kallo daya kafin yace komai Aunty tace "Har ka dawo Sadeeq" yace "Ehh na dawo, ina yini" tace "Lafiya lau" Mariya tace "ina yini ya Sadeeq" yace "Lafiya lau" Imaan ta sunkuyar da kanta, yana kallon Mariya yace "Bakuwa kika yi" Mariya tace "Eh yaya, classmate dita ce Imaan" Yace "Oh I see, sannu da xuwa bakuwa...." Imaan ta kasa dago kanta tace "Ina yini" yace "Lafiya lau" Daga haka ya juya ya fita, Imaan na kallon Mariya tace "Xan tafi Mariya" Turaren Humra mai yawa Aunty ta dibar ma Imaan da smart collections, Mariya ta amsar mata tana godiya, Imaan tayi mata godiya ta mike suka fita tare da Mariya Aunty na cewa ta gaida ummanta, Bedroom din Mariya Imaan ta shiga daukan jakarta da ledan shopping dinta, bayan ta dauka tana facing Mariya tace "Waye wannan da ya shigo Mariya?" Mariya tace "Wai ya Sadeeq? Yayana ne shi" Imaan ta xaro ido da sauri tace "Da gaske?" Mariya tace "Kin san sa ne?" Da sauri Imaan ta girgixa kai tace "A'a tambaya kawai nake" Mariya tace "He is my stepbrother, ga bangarensu can, kina shigowa compound part dinsu xa ki fara gani" Imaan tace "Ayya, ni dai xan wuce kar Ammi ta fara kirana" daga haka ta fita Mariya na biye da ita, a parlor suka tadda Aunty da Sadeeq, da fillanci Mama ke ce ma Sadeeq tunda fita xai yi ya daure ya ajiye Imaan ko bai kai ta har gida ba, Imaan tayi murmushi tace "Aunty ya bar shi xan hau napep" Mariya ta fashe da dariya, Aunty tayi murmushi tace "Ashe dai kina ji, kin bar kawar ki a baya, ba abinda ta iya sai shashanci" Imaan ta kalli Mariya da ta cinno baki tana murmushi, Sadeeq ya mike yace "Toh bari in ajiye ta" Imaan ta d'an xaro ido, Babu yanda ta iya, bata kuma yi ma mahaifiyar Mariya musu ba, suka fita tare da Mariya dake rike da ledan ta bayan Sadeeq ya fita parlorn, Aunty ta bi su har bakin kofa tana ce mata ta gaida ummanta, cikin motar suka tadda Sadeeq, Mariya ta bude mata front seat Imaan ta sunkuyar da kanta ta shiga ba don ta so ba, Mariya tace "Byee Friend sai mun hadu schl gobe, nagode sosai" murmushin karfin hali Imaan ta mata bata ce komai ba, Mariya na kallon Sadeeq da ya tada mota tace "Ya Siddiq drive my friend carefully fa" wani kallo yyi mata bai dai ce komai ba yyi horn, Mariya ta koma ciki tana dariya, har suka hau saman titi babu wanda yace komai cikinsu, bayan wani lkci yace "Wani anguwar xa ki?" Tana wasa da fingers din ta tace "Malali" bai ce komai ba, sai da suka kusa bayan kusan minti sha biyar sannan yace "Wani layin?" Ta gaya masa, daga nan kuma ta dinga nuna masa Inda xai bi har suka shigo gate din layinsu, dai dai gidan ta nuna masa yayi parking ya juya yana kallonta, bata yarda ta kallesa ba tana daukan ledanta dake kan kafarta tace "Nagode" yace "Welcm" daga haka ta bude motar ta fita ta rufe masa motarsa ya bi ta da kallo, Tsaye taga Mujaheed bakin gate da alamar fita xai yi don makullin motarsa na hannunsa, ya kalleta ya kalli motar ya sake kallonta da wani expression, ta wani daure fuska duk da faduwan da gabanta ke yi abinda yayi ma Maimoon ranan don an ajiye ta a mota ya fado mata a rai, turo baki tayi ganin ya ki matsawa daga gate din sai kallonta yake, ta raba ta gefen sa har tana bugesa ta shige gidan da sauri, juyowa yyi yana ci gaba da kallonta, tana ganin haka ta kwasa a guje xuwa part dinsu, sai da ta isa entrance din parlonsu ta tsaya ta juya tana kallonsa, har sannan kallonta yake, ta turo baki ta bude kofa ta shige ta kulle.🌟⭐ *Imaan* ⭐🌟 _By khaleesat Haiydar_✍🏻 9..... Bayan magrib Imaan ta je kai ma inna abinci ta hadu da Yusuf a hanya yana dawowa daga bangaren innan, gaishesa tayi ya amsa yace "Wai ina tsaraban shopping dina ne Imaan?" Tace "Body spray da turare na siya fa, ka xo sai in baka daya idan yyi rabi sai ka maido min, rabi kawai xan baka dama" yayi murmushi yace "Toh an gama, yaushe xaki fito part din inna?" Tace "Ina kai mata xan dawo" yace "Toh idan na dawo masallaci xan shigo sai ki fiddo min su in xabi wanda nake so" tace "Tohmm ina jiranka" daga haka ta wuce, Mujaheed ta gani bakin tap din inna yana alwala, taji muryar innar tana cewa "Mujaheed ka tabbatar ka datse min pampo wllh cutata kawai Imaan take ta debe min ruwa ta kai ma uwarta" Imaan ta murguda baki tace "Tunda Imaan kadai ce a gidan ba" Ta gefen Ido Mujaheed ya kalleta daga durkushen da yake, ta yi watsi da takalmanta nan bakin kofa ta shiga parlon ta dungure mata warmer din hannunta, inna ta daga murya tace "Har gwara Ita Mujaheed a kan su Ummi da Maimoon tunda ita tana tambayata kafin ta diba, su dai diba kawai suke da hakkina" Juyawa Imaan tayi ta fice mata a parlonta, bata ga Mujaheed din a bakin tap din ba kuma bai kulle mata ba da kwadon da tace Ga, ta yi wucewarta, tayi nisa sosai daga part din inna xata dauki hanyar part dinsu ta ga Mujaheed a tsaye, xaro ido tayi ta juya xata gudu ya cafkota, a tsorace tace "Wayyo me nayi maka" yana mata wani kallo yace "Uban wa ya ajiye ki a mota daxu? Ta 6ata fuska tace "Ni yaushe kaga an saukeni a mota, kawai fa...." wani wawan mari ya xabga mata, ta dafe kuncinta a rude ta fara kwala ma Inna kira, yana mata mugun kallo yace "Baxa ki gaya min waye shi ba" Kuka kawai take tana bubbuga kafa har sannan hannunta na dafe a kuncinta, strictly yace "Gobe na sake ganin haka wllh sai na faffasa maki jiki, duk gidan nan wa kika ga ana ajiyewa a mota, yar mitsitsiya dake xaki shiga mota a sauke ki a gida baki tsoron kowa ke gaki kwai da ake lallabawa" yana kai wa nan ya turata yyi wucewarsa, da gudu ta koma sashin inna ta shige parlon ta xube kasa tana rusa kuka, Inna ta mike tace "Ae fa an kwan biyu ba ayi ba, to uban waye ya ta6a min ke?" Cikin kuka sosai tace "Yaya ne" Inna tace "Waye haka? waye kuma wani yaya?" Imaan ta ki cewa komai sai kuka, Inna tayi fici fici da ido tace "Shi Mujaheed din ya sha wiwi ne da xai kai hannunsa jikin ki?" Imaan na shessheka tace "Mari na yayi ya tura ni" inna ta gwalo ido tace "Mari? Kika sakar masa fuskar ya mara baki ciccijesa kin gudu ba, uban me kika mashi? Toh ya tara kuma ya samu, ba a ta6a ki ba ma ya aka kare da ciwace ciwacen ki balle an mareki a fuska, to mu je ki nuna ma ubansa fuskar" tana fadin haka ta daga Imaan suka fice parlon, inna na tafe tana kunduma masa duk xagin da ya xo bakinta, Imaan dai sai ajiyar xuciya ta ke saukewa tana biye da ita, inna ta tura kofar parlon Abba bayan ta shiga main parlor, Umma ce duke tana sa turaren wuta a parlon, Inna ta wani hade rai tace "Ke ina mijin ki?" Umma ta dauke kai tana ci gaba da abinda take tace "Bai dawo masallaci ba, ina wuni" inna ta xauna saman kujera tace "Ina wuni kuma, dama da ban wuni ba kya gan ni Rukayya" Umma dai bata ce komai ba, Inna na kallon Imaan dake tsaye tace "Toh ai sai ki xauna mu jira ubansa koh" Imaan ta xauna kasa tana goge hawayen idonta, Abba ne ya fara shigowa parlon, yayi still ganin Inna, ta kafesa da ido tana girgixa kafa, yace "Lafiya kuwa inna?" Mujaheed dake bayan Abba har ya sako kai jin abinda Abba yace xai koma baya da sauri suka yi ido hudu da inna, da sauri cikin daga murya inna tace "Rikosa Ahmadu rikosa, abu ya lalace idan ya gudu kar ka bari ya fita, xamansa muke a nan" Abba ya juya yana kallon Mujaheed da ya wani hade rai ya fasa komawan, Abba ya karasa cikin parlon ya xauna yana kallon Imaan da ta hade kai da gwiwa sannan ya kalli Inna, Mujaheed na satan kallon Umma ya shigo ya nemi waje ya xauna a kasa, duk ya fi jin ummar tasa a kan inna, banda faduwa babu abinda gabansa ya ke, Abba yace "Me ya faru kuma inna" Inna ta kalli Umma dake tsaye tace "Toh Malama xa ki iya ba mu waje in yi sirri da d'a na koko mu koma daya parlon" Umma bata ce komai ba, Inna tace "Atoh ke kadai ce bare, nan d'a na ne da jikokina" Umma ta nufi kofa fuskar nan nata a murtuke, Mujaheed ya sauke ajiyar xuciyan samun relieve daya wato fitar Ummarsa, Inna ta mike da kanta ta rufe kofar har da sa makulli ta dawo, Abba dai sai kallonta yake, ta xauna tayi kicin kicin da fuska tace "Ahmadu daxu Imaan taje kai min abinci bayan ta ajiye ta fita ba sai wannan yaro Mujaheed ya kamata a hanya ya daddage ya kwada mata wani mahaukacin mari a fuskarta ba" tana fadin haka ta dago kan Imaan tana nuna ma Abba fuskar tace "Yanxu fisabilillahi meye wannan Ahmadu, yau ko dabba Mujaheed ya samu xai maresa haka balle d'an mutum, d'an mutum din ma 'yar kanin ubansa, to wllh ka dau mataki yanxun nan, Sam baxai yiwu ba, yarinyar da ake kaffa kaffa da ita saboda lalurorin da Allah ya saukar mata, yanxu gobe ba abun mamaki bane a ga fuskar ya salu6e wannan irin bugun da yaji, tunda ga irin yanda Allah yayi ta ko ina ba kwari sae laushi, to wllh ka san abun yi Ahmadu, shegiya nake idan na yadda" Mujaheed dai ya kasa dago kai sai kallonsa Abba yake, fuska daure Abba yace "Kai..." Ya dago da kyar, Abba yace "Uban me tayi maka ka kai hannu fuskarta?" Inna ta gyara xama ta hade girar sama da ta kasa tana kallonsa, Mujaheed yyi kasa da murya yace "Abba gani nayi an sauketa a mota daxu...." Abba ya kalli Imaan yace "Mota kuma?" Inna ta buda ido sosai tace "Mota?? Ina kika samo mota Imaan?" Imaan ta ki cewa komai ta fara hawaye, Abba yace "Baxa ki bude baki ki ma mutane magana ba, wa ya sauke ki mota Imaan?" Inna tace "A'a dakata Ahmadu kada a wani fake da an sauketa a mota a shashantar da xancen mari, kai ko daukanta aka yi a hannu aka sauketa a kofar gida bai kai katon d'an ka ya xabga mata mari har haka ba, a kan me? To an sauketa a motar, ita yarinya ce ko ba ta isa a ajiyeta a mota bane? Idan sabon saurayi tayi fa, ko dama haka xata yi ta xama ba saurayi?" Daga Abba har Mujaheed kallon inna kawai suke, ta ja tsaki tace "Wannan ai abun farin ciki ne ni dai a gu na, to da a mashin roba roba ku ka so a sauketa idan ba a mota ba, ko kuma idan tayi ta xama ba saurayi Mujaheed din ne xai aureta? Yau naga abinda ya isheni bai ishi Allah ba, kawai yaro ka tattakure ka kama yar mutane ka falle da mari ga ka mugun tantiri ko? sannan na taso takanas na kawo kara gun ubanka ya wani fake da wa ya sauketa a mota salon maganar marin ya bi iska, To Allah ya Isar mata" daga haka ta mike tana kallon Imaan tace "Tashi mu je, Allah dai ya isa" Tashi Imaan tayi ba tare da ta yarda ta kalli Abba ba inna ta ja hannunta ta nufi kofa tana cewa "Ka ci gaba da daure masa kugu wllh duk randa xuciya ya kwasheni idan ban sa k'attin anguwar nan sun tare sa a lungu sun nakada masa shegen duka na biya su ba kace ba uwata ta haifeni ba" da karfi ta rufo masu kofar bayan sun fita, Abba ya sauke ajiyar xuciya yana kallon Mujaheed, lkci daya ya hade rai yace "Does that warrant you to slap her Muhammad?" Mujaheed ya kasa cewa komai, Abba ya masa tsawa yace "Ba da kai nake ba malam?" Da kyar yace "Abba kayi hakuri, I was only trying to do what I thought was right, duk gidan nan nasan you don't tolerate yarinya ta shiga motar saurayi" Abba yace "Not to the extent of slapping her, if she proved to be stubborn why not report her to me? Kasan halin grandmother din ku, kuma kasan dole sai taje ta gaya mata" Mujaheed yace "Kayi hakuri" Abba yace "Stupid ba ni xaka ba hakuri ba, ita da ka mara da innan xaka ba hakuri, kuma kada ka sake wannan wawancin" yace "In sha Allah Abba" Abba yace "Idan ba hauka ba ma kawai ka daga hannu ka mari mace?" Shiru Mujaheed yyi, Abba yace "Tashi kaje kayi abinda na ce maka, ita kuma Imaan din xan hadu da ita" mikewa Mujaheed yyi ya kara ba Abba hakuri sannan ya fita parlon. A hanya Inna ta kalli Imaan tana washe baki tace "Ke kice saurayi me mota kika yi Imaan?" Imaan ta turo baki bata ce komai ba, Inna tace "Toh baki ce masa kakarki na nan da rai bane naga bai shigo ba, ko yaushe yace maki xai shigo gaisheni?" Imaan tace "Ni fa ba saurayi na bane, driver din gidansu kawata ne naje dubota bata da lafiya shine mamansu tace ya maido ni gida" sake baki inna tayi a sanyaye tana kallonta tace "Ba lafiya... Direba kuma?" Imaan bata ce komai ba ta shige balcony dinsu ta bude kofar parlor ta shiga sai a sannan ta kalli inna dake tsaye baki sake har sannan tace "Sai da safe" daga haka ta kulle kofar ta sa makulli. Washegari da ya kasance Friday tun da Imaan ta dawo schl take xaune balcony dinsu tana assignment dinta na maths, Ammi ta kwalo mata kira for the second time ta ajiye pen din ta amsa, Ammi tace "Idan baxa ki ci abincin ba ki shigo ki mayar min kitchen nace" Tace "Ammi fa na kusa gamawa saura biyu" Daga haka ta ci gaba da assignment din, kamar ance ta daga kai taga wata budurwa da baxata wuce shekaru ashirun da biyu ba tana tahowa, xaro ido tayi ta ajiye pen din ta mike ta fito tace "Lahh Anty Farida" murmushi kyakkyawar budurwar tayi tace "Imaan ta mance ni" Rungumeta Imaan tayi tace "Wllh ban mance ki ba Anty farida, yaya ne yanxu baya bani waya mu gaisa" Farida tace "Toh ke ba sai kice ya ba ki ba" Imaan ta tabe baki tace "Ai to yanxu babu ruwana da shi shima ba ruwansa da ni" dariya Farida tayi tace "Toh saboda me" Imaan na murmushi ta amshi ledan hannunta tace "Ae yanxu yaya ya xama mugu, wajen inna xa ki?" Farida tace "Ehh na xo layin kusa da wannan ne nace bari in shigo yau dai mu gaisa da inna" Imaan tayi dariya tace "Amma yaya yasan xa ki xo?" Farida tace "A'a bai sani ba" Imaan tace "Last time da kika xo gaida inna ai tare ku ka je da shi to me yasa yau ma baxa ki bari ku je tare ba?" Tayi murmushi tace "Na fa ce maki bai ma san na xo anguwar ba, Ammi tana ciki?" Imaan tace "Ehh tana ciki" Farida tace "Toh bari mu gaisa" daga haka ta nufi parlon Imaan na biye da ita, Da fara'a Ammi ta tarbeta tace "Kin guje mu Anty Farida" banda murmushi babu abinda take tace "Ammi karatu ne wllh, kinga yanxu ma hutu na xo" Ammi tace "Allah sarki, Allah ya bada sa'a, ya kuma bada abinda aka je nema" Farida tace "Ameen Ammi" daga haka tayi mata sallama tace "Xan je mu gaisa da inna" Ammi tace "Toh idan xa ki wuce ki biyo ta nan mu yi sallama" tace "Toh Ammi" daga haka ta mike imaan na kallon Ammi tace "Ammi ni dai xan rakata gun inna, idan na dawo xan ci abincin" Ammi tace "Ai shi kenan" tare suka fita da farida tana rike da ledan ta, farida budurwar Mujaheed ce babu wanda bai sani ba a gidan, 2 years back kafin Ummarsa ta dawo gidan farida kan xo ta gaida Ammi da Anty, idan ko xata je gaida inna dama shi xai rakata kuma ko minti biyar baya yarda su yi a parlorn kafin inna ta fara xance yake janta su fita, sosai farida ke son Imaan tun lkcn da take xuwa gidan lkcn ma bata kai haka ba, suna isa bangaren inna imaan ta bude kofar ta shiga da sallama, Maimoon da Rahma na parlon xaune tare da inna, Farida ta shiga da sallama, inna dake xaune kan tabarma ta amsa tace "Wacece wannan kuma?" Maimoon tace "Lahh Anty farida sannu da xuwa" farida tana murmushi tace "Yauwa Maimoon, ykk" durkusawa tayi kasan rug tana kallon inna tace "Ina yini Inna" Inna tace "Lafiya lau ni dai ban gane ki ba" Maimoon tace "Inna faridar ya Mujaheed ce fa" Inna tace "Ayyoo farida ce, sannu da xuwa, kai ku kawo mata ruwa da sauran ayaban nan" Imaan ta mike ta dauko mata ruwa, Inna tace "Allah sarki, da yake sau uku ya ta6a kawo ki a gurguje shi sa ban gane ki ba, ya iyayen naki?" Tana murmushi tace "Sun ce a gaida ku inna" Tace "To madallah muna amsawa, Mujaheed din ne ya kawo ki kenan?" Farida tace "A'a ni kadai na xo" Inna tace "Atoh ba dole ki xo ke kadai ba, ni ma duk yau ban gansa ba ko gaisuwar Juma'ah ma bai xo ya min ba daga na kai kararsa kan ya doki yar kanwar nan ta sa, ko ke haka yayyinki ke cutar ki?" Murmushi kawai farida tayi, Inna tace "Toh Mujaheed kam cutan nasa kannin yake, kawai daga an sauke yarinya a babban mota ya daddage ya kwada mata mari ba laifin fari balle na baki wai ashe ma gantalallen direba ne ya sauketa, to kin san sa da xuciya sai dai kiyi ta hakuri kawai, dama tun da aka haifesa na ji irin kukan da yake a asibiti nasan akwai bala'i gaba, baki ji ba duk ya cika asibitin da muryarsa ga shi wani lafcece" Imaan ta fashe da dariya har da kyakyatawa Maimoon na taya ta, Rahma dai ta6e baki kawai tayi, Farida kam sai murmushi take kanta a kasa, Inna tace "Wllh ba xancen dariya ba nasan abinda nake fada, kuma a yunwace aka haifesa, kilan dai uwar bata ci abinci ba taje haihuwarsa, mu dai haka muka koma gida na wanke sa tass, baki gansa ba jazur da shi ba yanxu da ya kode ba, ke kinga wahalar da nayi da Mujaheed wllh k'are baxai ci ba, tun fa yana tsummarsa nake wahala don sai da nayi kwana hamsin ina kai komo a kansa, to ba abinda uwar ta iya har na koma gidan mijina, daga nan kuma sai dai in kai masu ziyara duk sati, lkcn baki ga uwarsa ba yar siririya doguwa kamar dai yanda kika ga wannan yarinyar Imaan" Inna na yamutse fuska tace "gashi uwar tayi ta cika masa nono yayi ta bulbula tumbudi duk k'arni malam, duk jikokina babu wanda yyi tumbudi kamar Mujaheed, ni ne ma nace uban ya sa masa Mujaheed" Imaan dai an samu abinda ake so don har wani kwanciya kasa take don dariya, Maimoon kawarta na taya ta, Farida dai ta kasa dago kai, Rahma ta wani hade rai tana hararan Inna ko Kadan bata ga abun dariya a wajen ba, Inna ta gyara xama tace "Lkcn yana da shekara daya da wata bakwai uwar ta yayesa, shi ma fa da kyar, ai duk cikin 'ya yan Ahmadu babu wanda ya sha nono irinsa, ya tsotsi uwar ba kadan ba, ko ke baki ga bakinsa d'an tsiyot kusan a tsuke ba? Ai duk tsotso ne yaja haka, sai yaje gantalinsa ya dawo ki ji yace Nono, uwar sai ta fiddo ta basa ya sha yyi nak sannan ya mayar, ke in takaice maki da kyar kanwar uwar ta yayesa don ni dai nace baxan iya wahala ba cikin kishiyoyi, ae ko sai kinga tashin hankali gunsa, bayan an yayesa kuwa idan Mujaheed ya daga maki roban yoghurt to bai direwa sai ya kwankwade tass, ga katon ciki yanda kika san an kifa masa kwarya, Sai uban kukan banxa da shagwaba, ni dai ba komai yasa na daukesa gaban uwar ba sai ganin xai hallaka, yo hallaka mana katon yaro haka yayi fitsari a tsaye kashi a tsaye uwar sai dai ta kwashe ta rabu da shi, duk ta dau son duniya ta daura masa, Shi kuma lkcn kaninsa isuhu na cikin tsumma an haifesa wani fiyot da shi kamar kyanwa ni na ma xata bakwaini ne" Shiru Inna tayi tana kallon Imaan, can ta xaro ido tace "Auzubillahi... Ke meye haka kike yi?" Maimoon ta tsayar da dariyar da take tana kallon Imaan, da sauri ta dagota tana xaro ido tace "Me ya faru Imaan?" Farida ma ta tashi da sauri ganin yanda numfashinta ke sama, inna ta mike a rude tace "Kun ga xata ja min jalala ina xaman xamana ko, to ita nake ba labari da xata dinga dariya haka taje ta mutu a banxa a buga ni a jarida? kai ku fitar min da ita kar ace a parlo na ne, meye kuma numfashi na neman daukewa daga ina ba yarinya da ta xo gaisheni labari? Ni dai ba ruwana a kai ta gun uwarta, ni wllh ba ita nake ba labari ba" Da gudu Maimoon ta mike xata je dauko mata inhaler suka kusa cin karo da Mujaheed xai shigo parlon, ya turata yace "Baki da hankali ne" kamar xata yi kuka tace "Ya M.A Asthma din Imaan ne...." daga haka ta fita, Da sauri ya karasa yana kallon Imaan yace "What happened" inna da har ta fara matsar kwalla tace "Ka fita da ita Mujaheed idan ma asibiti ne ku tafi, wllh ba ita nake ba labari ba xata sa ni a bakin duniya ni ban ma san lkcn da ta shigo parlon ba" Mujaheed ya kalli farida da mamaki, inna tace "Ka rufa min asiri ka fita da ita Mujaheed, meye kuma dariya haka kamar mahaukaciya, ban san meye abun dariya a xance na ba" dagata Mujaheed yyi suka fita parlon, can kusa da wani flower ya xaunar da ita yana kallonta yace "Relax now" da kyar take numfashin kamar xai dauke, Maimoon ta iso kusa da su ta durkusa ta mika ma Mujaheed inhaler din, budewa yyi ya kai bakinta da sauri, bayan wani lkcn ta dinga sauke ajiyar xuciya, maimoon dai sai kallonta take cike da tausayi, Ta jingina da flowern tana ajiye numfashi a hankali hawaye na sauka idonta cikin tsarkewar murya tace "Yaya xan sha ruwa" mikewa Maimoon tayi ta tafi dauko mata ruwan da sauri, shi dai kallonta kawai yake, bayan wani lkci ta daga kai suna hada ido ta kamo hannunsa ta kwashe da dariya, ya daure fuska yace "kina da lafiya kuwa?" Tana dariya a hankali tace "Wllh yaya babu abinda inna ta mance bata gaya ma Anty farida ba yau" ya wani xaro manyan idonsa yace "Kamar me?" Imaan ta kara fashewa da dariya hawaye na sauka idonta, ya hade rai yace "Baxa ki daina wannan dariyar mahaukatan ba" ta hadiye da kyar, har wani ciwo kirjinta ke mata cike da karfin hali tace "Labarin ranan da aka haifeka har sanda aka yaye ka take bata da yanda...." Ganin yanda Mujaheed ya bude baki da idanuwa yasa ta kara kwashewa da dariya tace "Wllh yaya har da tumbudi da fitsari da kashi duk ta fada mata" Mujaheed ya kasa rufe baki, Ganin irin dariyar da take ya sauke boyayyen ajiyar xuciya yace "Toh dariyar ya ishe ki haka" Mikewa yyi fuska daure xai koma part din Inna ya hangota tana tahowa da gudu, tsayawa yyi har ta iso yace "Gaskiya Hajiya ki daina abinda kike yi a gidan nan, ke dai magana magana magana baya kare maki, wanda ya kamata da wanda bai kamata ba haba don Allah, ni bana son irin wannan abun, ki shekara kina bada labarin kowa amma banda nawa, ba ruwanki da rayuwata da yanda aka haifeni ke kenan kowa kice xaki ba labari baki san bako ba, kawai ke dai kiyi ta magana babu naxari haba don Allah" sake baki tayi tana kallonsa, mikewa Imaan tayi tana hadiye dariyarta sum sum xata bar wajen inna tace "Ke dai wannan 'ya ta Bukar anyi munafuka wllh, to da kika gaya masa dukana xai yi ko ko, ina ce yarinyar da xai aura ce, kuma laifi ne don na bata labarinsa? Me yasa ban samu masu gadi na basu labarin ba? Saboda bai shafesu ba, komai fa da ku ke gani a rayuwar nan kamawa yake, yarinya ta xo gaisheni sai in xauna muna kallon kallo da ita??" Imaan ta turo baki tace "Ba wani nan, yaya har ce mata ta yi da yunwa aka haifo ka duniya kana ta ihu a asibiti, kuma saboda shan nono bakin ka ya xama d'an karami haka, wai sai kaje yawo ka dawo sai ce ma Umma nono sai ta baka ka sha, shi ma ya Yusuf sai na gaya masa tace an haifesa fiyot kamar kyanwa kamar bakwaini" Girgixa kai Mujaheed yyi ya bar wajen a mugun fusace Imaan ta bi bayansa da gudu tana kyalkyala dariya, Inna ta share kwallar idonta tace "Ni dai ba don gabana aka haifi muguwar yarinyar nan ba wllh sai ince ba jininmu bace, don gulmarta ya wuce hankali ya dauka, banda haka yaya xa ta dinga hada mutane fada a gida haka, shi kenan ni kuma bani da Ikon bada labari, ni daga yau ma kar ta sake xuwa min na yafe abincin, yarinya dai guda daya sai hada bala'i a gida, gashi ta hadani da Mujaheed xata tafi ta hada ni da isuhu kuma, ni dai bari Ahmadu ya dawo a ja mata kunne kar ta sake xuwa min, Bukar dai ya Haifi jaraba" Kindly patronize ur writer for continuation, tnx 07087865788.A fusace Mujaheed ya juya ganin Imaan na bin sa yace "Kee Why are you following me?" Ta xaro ido tace "Ni ba gidanmu xan tafi ba toh??" kwafa yyi ya ci gaba da tafiyarsa tana kai wa bangarensu ta shiga tana dariya kasa kasa. Sai kusan karfe biyar Farida ta fito bangaren inna bayan ta cikata da abun arxiki, su sabulai, omo, malt har da bottle water duk ta xuba mata a leda, Inna ta rakota har bakin kofa tana cewa "Toh sai ki gaida iyayenki kinji, Allah maki albarka, nagode nagode, naji dadin turaren da kika kawo min duk da dai ba mai tsada bane, sai ayi ta hakuri da Mujaheed dai, Allah kuma ya nuna mana lkcn abun arikin nan" murmushi kawai Farida take ta wuce tare da Maimoon dake rike da ledan da inna ta bata, sai da suka isa bangaren su Imaan tace "Bari na shiga in duba imaan" Tare suka shiga parlon da Maimoon, imaan dake kwance tana kallo ta mike xaune tana murmushi tace "Har xa ki tafi Anty farida" farida tace "Eh xan wuce ya jikin fa?" Imaan tace "Ae na ji sauki" Farida tace "Toh Allah ya sauwake xan fito daxu inna tace kun tafi asibiti da Mujaheed" dariya imaan tayi tace "Ni dai naji sauki" farida tace "Toh ki dinga yawo da inhaler din ki amma" Imaan tace "Toh nagode" Ammi ta fito daga daki tace "Har xa ki tafi Farida" farida tace "Ehh Ammi yamma yayi" Ammi tace "Toh mun gode da ziyara, ki gaida mamarki da mutan gidan kin ji" farida tace "In sha Allah xa su ji" body spray uku Ammi ta sa mata a leda, ta amsa tana godiya suka fita tare da Imaan da ta sa hijab xa ta rakasu, xaune suka tadda Mujaheed a part dinsu kusa da parking space a kan farin kujera idonsa a kan wayar hannunsa, farida na daga inda take ta gaishesa ya kalleta sannan ya mike yace "Why did you come without telling me?" ta d'an buda ido tace "Saboda baka son inna ta bani labarin ka? To yau duk naji komai" Dariya Maimoon tayi har da imaan ya watsa masu wani kallo fuska daure, Farida tayi murmushi tace "Kawai na xo anguwar ne shine nace bari in karaso in gaida inna" yace "But da rana ai mun yi waya kuma baki ce kina anguwar ba" tace "Noo ban taho ba lkcn, nima fa ban san ma xan fito ba, I came on an errand for my mum" Kamar ance Mujaheed ya daga kai ya ga Ummar sa tsaye a balcony na sama tana kallonsu keenly, farida ta kalli sama ita ma, ganinta ta sunkuyar da kanta, murya can kasa yace "I think you have to go in ku gaisa tunda ta gan ki" Tace "Toh" imaan tace "Toh Anty farida sai wani lkci xan amshi number dinki gun yaya idan xai bani" ta gefen ido ya harareta, farida tace "Toh shi kenan imaan na gode sosai" Daga haka ta wuce Maimoon tayi leading din farida xuwa parlon Umma, Umma na xaune wayar ta a hannu suka shigo, Farida ta durkusa kasa tana kallonta tace "Ina yini Umma?" Murya can ciki umma tace "Lafiya lau" Farida na wasa da fingers dinta tace "Ya aiki umma" umma tace "Alhmdllh" shiru farida tayi, Maimoon dai na tsaye sai tabe baki take, Umma tace "Ya 'yan gidan naku?" Farida tace "Suna lafiya" Umma tace "To yayi" bayan kusan minti biyu farida ta mike tace "Toh xan koma umma nagode" umma tace "Toh a gaida gida" daga haka ta fita Maimoon na biye da ita, dakin Anty suka shiga, Anty taji dadin ganin ta, bayan sun gaisa ta tambayeta mamarsu farida tace "Suna lafiya Anty" Da ta tashi tafiya Anty ta bata dubu daya kudin transport, Maimoon ta amsar mata don kin amsa tayi suka fita dakin Anty, Mujaheed na tsaye parking space suka fito gidan, bayan sun iso inda yake yana kallon farida yace "Gida xa ki koma yanxu?" Tace "In sha Allah" yace "Ohk mu je in ajiye ki" har ya bude mota wayarsa ya fara ring, ya duba yaga umma ce ke kiransa, a hankali ya daga ya kai kunne, Umma tace "Ina jiran ka parlor yanxu" yace "Toh" daga haka ta katse wayarta, ya kalli Farida a hankali yace "Bari in baki transport kawai dear, akwai aikin da xan yi yanxu" daga haka ya fiddo dubu biyu ya mika mata, ta girgixa kai tace "A'a ka bar shi I have transport thanks" ya mika ma Maimoon yace "Ki bata plss" Maimoon ta amsa, yana kallon faridar yace "Sai mun yi waya dear" daga haka ya wuce ciki. Maimoon ta tabe baki tace mu je Anty farida. A hankali Mujaheed ya bude kofar parlon Ummarsa ya shiga da sallama, tsaye ya sameta ta rungume hannu tsakiyar parlon wandering about, ya karasa yace "Umma gani" kallon da ta dinga masa ya sa ya durkusa ya sauke kansa kasa, tace "Mujaheed dama ban raba ka da wannan yarinyar ba?" Ya kalleta da kyar yace "Umma ni ban fa san da xuwanta gidan ba, kuma...." Sai yayi shiru, Fuska a murtuke tace "Kuma me?" Yace "Umma don Allah me yasa baki so na da farida?" Tace "Ra'ayi! Wato dai har yanxu kuna tare duk jan kunnen da na maka kwanaki koh? To wllh ka kiyaye bacin raina Mujaheed, ka kiyaye ni a gidan nan, uban me xaka yi da diyar talakawa ka ja min bala'i, in xama abun magana gun kawayena, duk fadin kaduna ka rasa budurwar da xaka nema sai wannan yar, warce iyayenta ke xaune a ghetto ? Haba Mujaheed are you even alright?" Yace "But Umma I see nothing wrong with that, arxiki fa na Allah ne, beside suna da rufin...." Umma ta dakatar da shi rai bace tace "Da ca nayi arxikin na kanin ubanka Sadeeq ne? Ni xaka ma wa'axi? To wllh in dai kana son kwanciyar hankalin ka a rayuwa ka fita harkar yarinyar nan, su je can su samu wani kuma, abubuwan alkhairi da ka dinga masu a baya da ciyar da su da ka dinga yi Allah ya saka maka da alkhairi, ina ji ina gani baxa ka auri yarinyar nan ba ka xama mai bada charity su talautar min da kai, yarinya dai dai class dinka in sha Allah xan samo maka tunda naga ba saiti gareka ba, ba abun mamaki ba wataran ma ka xo min da yar talla kace ita kake so, kai ko kunyan kanka ma baka ji, dubi yarinyar da Yusuf yake nema xar sha'awa yar masu kudi ta ma fi ubansa kudi shi ne kai xaka makale ma yar ghetto ko, to wllh ka guji bacin raina a gidan nan, sannan don munafurci da kinibibi ta shigo sumui sumui ta nufi gun alakakan kakarka da ba so na take ba a gidan nan salon duk ta bata ni gunta ta hure mata kunne, don wllh da ban ganta a sama ba dama bata yi niyyar shigowa gaida ni ba, ta kama ta tafi gun kakarka da kanwar uwarka Aisha tunda ita ta haife ka, Allah kadai yasan me kakar taka ta k'itsa mata, wato Mujaheed tarayyar ka da yarinyar ba abu bane mai yiwu wa samm kayi ta kanka tun wuri, daga this very moment na raba ka da yarinyar na har Abadan abidina, tashi ka ban waje mara tunani kawai" mikewa yayi bai ce komai ba ya nufi kofa ta bi sa da harara har ya fita ya kulle mata kofar ta. Xaune yake cikin Lafiyayyen motarsa nesa da gidan, abokinsa dake gefensa yace "Look ni fa na gaji da xaunar da ni da kayi cikin mota tun daxu Sadeeq..." Sadeeq ya shafa cute Beards dinsa a hankali yace "You just chill Fahad... jikina na bani xata fito soon" Tabe baki abokin yyi yace "Have you changed ur mind about loving and dating only whites?" Sadeeq ya xaro ido yace "Of course No, wannan fa yar yarinya ce.... I think she is not even up to 18, she is....." Sai kuma yyi shiru yana murmushi, Fahad da ya saki baki yana kallonsa yace "Sweet eighteen kenan" Yar dariya Sadeeq yyi a hankali underneath his breathe yace "she is beautiful" Fahad yace "and why didn't you callect her digit?" Wani kallon gefen ido yyi masa yace "Sai kace nine kai? How on earth xan amshi numberta bata ce in bata nawa ba" Bude gate da suka ji aka yi yasa duk suka daga kai da sauri, Mujaheed ne ya fito, walking majestically ya nufi motarsa da yyi parking a waje. Imaan na xaune bakin kofar kitchen tana ta yi ma Amminta dake girkin dinner hira, Ammi tace "Daxu inna ta xo fa wai tana nemanki idan kin dawo schl" Imaan ta xaro ido tace "Ni??? Ba ruwana baxan je ba, ce ma Abba tayi fa kar in sake xuwa mata ina kwasan maganganunta ina yadawa a gidan nan, ita gaskiya xata gudu ta bar gidan idan naje mata" Ammi tayi murmushi tace "Toh tace kwana biyu bata gan ki ba ko jikin ne" Imaan tayi dariya tace "Xa ma ta fadi gaskiya ne, ba inda xanje ta sake cewa na mata laifi gwara dai Maimoon ta ci gaba da xuwa tana kai mata abinci" Ammi tace "Toh ke xa ki kai yau, kina ajiye mata ki gaisheta sai ki fito ba shi kenan ba" imaan ta bata fuska kamar xata yi kuka tace "Ni dai Ammi nayi alkawarin baxan sake xuwa part dinta ba fa" Ammi dai bata ce mata komai ba. Bayan magrib Imaan na Idar da sllh Ammi ta tilastata kai ma inna abinci sabanin Maimoon da ta dinga xuwa tana kai mata kusan kwana uku kenan, Imaan ta dau abinci ta fita fuska daure kamar mai shirin yin kuka, tana isa bangaren inna ta tura kofar ta shiga, Yusuf ne parlon suna hira, Inna na ganinta ta washe baki tace "A'a takwara ce" imaan ta ajiye abincin ba tare da ta kalleta ba tace "Ina yini?" Inna tace "Lafiya lau, ni kwana biyu ban ganki ba nace to ko jikin ne? Duk hankalina ya tashi na tafi sashin ku daxu Aisha tace ai kin ma tafi boko" Imaan ta tabe baki tace "Lafiya ta qlau kawai dai umarnin Abba nake bi" inna tace "Umarni kuma? Umarnin me ya maki?" Imaan ta buda ido tace "Ba ce masa kika yi kar na sake xuwa bangaren ki ba baki son ganina, shine ai na daina xuwa" Inna ta kalli Yusuf tace "Oh oh Allah, isuhu kaji wata magana irin na Ahmadu ko, dama an san babba da hadin fada, ni yaushe muka yi haka da shi, daga nace yayi mata fada ta daina haka gidan aure xata kuma ba halin xaman gidan miji kenan ba, shine xai ce nace kar ta sake xuwa min? To ina da masu xuwa ne idan ba ita ba ko shi xuwa yake yi ya xauna min, ni dai a dinga jin tsoron Allah gaskiya" Yusuf yyi murmushi yace "Toh ba ga ta nan dai ta xo ba" Inna na kallon imaan tace "Ni ban yi haka da shi ba gaskiya, ga soyayyen naman ki can na ajiye maki tun jiya a daki, naki ne da na Mujaheed shima kwana biyu ban gansa ba sai ki diba naki ki bar masa nasa" Imaan ta turo baki ta wuce cikin dakin, daukan bowl din tayi ta bude taga soyayyen naman cow din sai kamshi yake ta xubawa, ta xauna gefen gado ta kirga gaba daya taga yanka sha takwas ne, murmushi tayi ta fita don dauko leda a kitchen, Inna tace "Kin diba naki" tace "Leda xan dauko a kitchen" daga haka ta shiga kitchen din ta dau leda biyu ta boye daya, tana rike da daya ta fito ta koma cikin dakin, equal ta raba naman ta debi nata, cikin sauran da ya rage ta debe guda hudu ta xuba a daya ledan ta ajiye sauran, ta window ta jefar da guda hudun da ta dauka sannan ta fito parlor, inna na kallon hannunta tace "In ji baki kwashe naman ba nace naki da na Mujaheed ne, don gaskiya nasan halin ki" ta xaro ido tana nuna mata ledan tace "Duba ma ki gani, guda sha takwas ne na kirga na dau tara na bar masa tara" Inna tace "Yauwa kinyi dubara" Yusuf da ke ta kallonta yana murmushi yace "Are you sure imaan" da mamaki ta kallesa tace "Me that don't even like eating meat sef" murmushi ya kuma yi yace "Eh naga alama" Inna ta tabe baki bata dai ce masu komai ba, Ummi ce ta shigo parlon rike da abinci ta kawo ma inna, inna ta bude warmer din ta girgixa kai tace "Mayar masu, ce masu aka yi xaman abinci nake a gidan nan shekaranjiya a ban shinkafa da miya jiya a ban dafaduka yau kuma a ban koren shinkafa, maida baxan ci ba" Yusuf yace "Toh ae ba iri daya bane wannan fried rice ne fa" Inna tace "Toh Isuhu ni kenan a cin shinkafa xan kare, wlh na gaji da kaddararren shinkafar nan, Ahmadun baya ajiye abinci ne" tana fadin haka ta jawo warmer din da Imaan ta kawo ta bude, shinkafa ce da miya sai salad a gefe shi ma, Yusuf ya fara dariya, Imaan ma ta kyalkyale da dariya, inna tace "Toh Allah ya mana tsari" tana fadin haka ta kalli Ummi tace "Ke Mujaheed ya dawo ne ko yana can yana siyar da abinda ya kasa a titi?" Ummi tace "Ya dawo, tare muke tahowa kuma ya tsaya yana waya " Bata rufe baki ba sai ga shi ya shigo da sallama, farar 3 quatre ne jikinsa da bakar riga, Inna ta tura kulolin gabanta tace "Mujaheed don Allah irin wannan tuwon da ka taba siyo min nake so ni dai" ya karasa parlon ya ajiye ledan fruits din hannunsa yace "Ae sun tashi masu siyarwan" tace "Ni dai don Allah ka rufa min asiri ka tafi, su tashi su je ina?? Bayan ga maza masu fita titi cin abinci ta dalilin rashin iya girkin matansu" Yace "Ki tambayi Yusuf da karfe shidda suke tashi" yana fadin haka ya bude warmer din abincin kusa da ita yace "Wannan kuma fa" tace "Haba Mujaheed shinkafa dai shinkafa dai inje basir ya cafke ni, wa nake da shi da xai nema min magani, wllh baxan ci shinkafa jiya in ci yau ba, wannan ai mugunta ce ma" Mujaheed ya tabe baki yace "Toh ai sai ki sha tea ki kwanta" Ta maka masa wani kallo tace "Kai xaka gaya min abinda xan yi ko raini?" Yusuf ya mike yace "Toh bari a samo maki tuwon idan basu tashi ba" daga haka ya fita, Inna tace "Toh Allah yayi maka albarka, Ya baka abinda kake nema duniya da lahira, to dama? idan ba kai ba waye, Allah dai ya ma albarka" Mujaheed ya kalleta ta gefen ido xai fita inna tace "Ga namar ka can a daki, baxan biye ta halin ka ba ni dai" Ya juyo yace "Nama na me?" mikewa Imaan tayi ta nufi kofa ta fita sum sum, inna ta bi ta da kallo baki bude tace "Toh kuwa idan ba wani ikon Allah ba ta kwashe rabon naka, Ummi tafi daki ki dauko min roban naman, ai ni naga abinda ya isheni bai ishi ubangijina ba" Ummi ta tafi dakin ta dauko bowl din naman inna ta amsa ta bude tana kallo ta saki salati ta ajiye ta rike ha6a, Mujaheed ya dau roban yana kallon sauran naman, inna ta sauke ajiyar xuciya tace "Ta kwashe wllh, gaskiya dai wannan 'ya ta Bukar bata da hali, muguwa ce ta innanaha, ni wllh da xaka burgeni Mujaheed ka bi ta har gaban uwarta ka kwato min namana gaba daya na fasa badawa" Ya ajiye bowl din hannunsa bai dai ce komai ba, Inna tace "Idan kuma baxa ka ba ni sai in tashi inje, ya xata kwashe min nama gaba daya bayan na mata bayani, naman fa yyi yanka kusan ashirin shine ta bar maka hudu, ni dai rabona da a sani magana haka tun kwana uku da suka wuce, to bata xuwa.... yau kuma ban san uban me ya kawota ba" Yace "Sai da safe" bai jira cewar inna ba ya fita parlorn, motsin da yaji a bangarensu Imaan yasa ya tsaya duk da bai yi niyyar tsayawa ba, durkushe ya ganta a balcony dinsu tana tattara shoes dake wajen xata shigar da su ciki, yana kara taku daya xata gansa saboda hasken dake wajen hakan ya sa ya tsaya, mikewa tayi ganin alamar xata fito ya koma baya da sauri ya tsaya jikin flowers, socks dinta da ta shanya take kwashewa, da sauri ya nufeta tana ganinsa ta saki takalman hannunta da socks ta gudu xuwa balcony dinsu, Amma tuni ya kamata ta xaro ido kamar xata yi kuka tace "Yaya me nayi kuma?" Ya daure fuska yace "Ina naman da kika kwashe" tace "Yaya nama kuma, ni fa guda shidda na dauka" yace "Dauko shiddan" tace "Toh ai rabona ne fa" ya mata wani kallo yace "Na fara wasa da ke gidan nan koh?" Kamar xata yi kuka tace "Toh tasan ba bani xata yi ba kuma ba ni ta ajiye ma ba meye na sa min rai, baxan sake xuwa parlonta ba ma" yace "Eh dauko naman" durkusawa tayi ta dau kayan da ta saki, tace "Mu je parlor in baka" yace "Baxan shiga ba ki dauko min" tace "Toh ni dai idan baka shiga ba baxan baka ba" ya wani daure fuska yace "Ke wai yaushe na xama mate din ki a gidan nan?" Tace "Toh xaka tsammin plss" ya fixgota yana mata wani mugun kallo har tana jiyo numfashinsa, Bata sake cewa komai ba yace "Tafi ki dauko min" a hankali tace "Toh" sannan ta nufi balcony din ya bi bayanta ya tsaya yana kallonta, ta bude kofar ta shiga sannan ta juyo tana kallonsa, wani murmushi tayi ta wara masa ido tace "Good night yaya" daga haka tayi banging kofar da sauri ta sa makulli, sosa kansa yyi bayan kusan second goma ya juya ya fita balcony din yana murmushi. Imaan ta fito daki jin Ammi na kiranta, da mamaki tace "Ammi ina xa ki kuma?" Ammi na rike da flat shoe dinta tace "Kin manta yau xa a kawo lefen Seeyama" Imaan tace "Ohh na manta, to ni Ammi baxan je in gani ba" Ammi tace "Toh girkin da na daura fa?" Shiru tayi kamar xata yi kuka, Ammi tace "Toh idan shinkafar ya nuna ki kwashe sai ki taho" Imaan ta washe baki tace "Toh" Ammi na fita parlon ta tafi kitchen da sauri tayi ta tsaye tana jiran dahuwar shinkafar, daga karshe da sauran ruwa a ciki ta kwashe a warmer ta fita da sauri, Hijab ta sa har kasa ta bar gidan xuwa part dinsu Maimoon, har an kawo akwatunan ta tarar masu kawo wa ma har sun tafi, Anty ce da kawayen Umma uku suka shiga buda tsadaddun akwatuna set shidda da aka kawo, Ammi dai na xaune parlon, parlon cike yake da mutane duk yawanci yan uwan Umma da Kawayenta, Imaan ta nufi inda Maimoon ke xaune duk suna jiran a bude akwatuna su fara ganin kaya ta durkusa, Umma dai fuskar nan babu yabo babu fallasa tana tsaye, Kanwar Umma Hajiya Mariya ce tace "Imaan fa an xama yan mata" Imaan tayi murmushi ta sunkuyar da kanta tace "Ina yini Mama" Umma ta wani daure fuska tana kallon kanwartata, Hajiya Mariya tace "Lafiya lau Imaan ya schl ko kun gama secondary din?" Imaan ta girgixa kai tace "A'a Mama muna ss1" Hajiya Mariya tace "Maa sha Allah, Allah ya baku sa'a" Umma na kallon hajiya mariya tace "Ban ga amfanin ki xaune nan ba Mariya da ki tashi ki bar nan kawai" Murmushi kawai Hajiya Mariya tayi ta mike nan suka dinga fiddo kayan akwatunan, Ammi dai bata tashi ba, Maimoon ta ja Imaan kusa da boxes din wai su ga kaya, Imaan na daga kaya taga wani arnen kallon da Umma ke mata, sunkuyar da kai tayi bata sake yunkurin matsawa kusa da boxes din ba, kaya maa sha Allah sunyi kyau sannan masu tsada, Hajiya Laraba tace "Kai maa sha Allah lallai Seeyama tayi goshi, Allah ya sanya alkhairi ya sa gidan xamana, Allah kuma ya nuna mana na sauran yan matan gidan haka" Umma tace "Toh Ameen amma kuma lafiyayyun yan matan gidan dai koh?" Kawayenta suka kwashe da dariya Anty ta daga kai ta kalli Umma, Wata kawar Umma tace "Gaskiya kam irin wannan kaya ai sai mai lafiya, Mara lafiya kam yyi fatan samun mijin kafin ya sa ran kaya haka" Umma tayi wani dariya har da shewa, Hajiya Mariya da mood dinta ya canxa ta dinga kallon yayartata, ita dai Ammi kallon kayan da suke ta fiddowa kawai take, Umma ta kalli kawarta Hajiya Shafa tace "Ya haka hajjaju naga baki tashi duba kaya ba ko kema kina cikin sahun yan yi ma 'ya ta bakin ciki ne naga dai duk kin aurar da naki yaran" dariya sosai Hajiya Shafa tayi tace "Masu bakin ciki sun san kansu, ni ko in rasa Wanda xan ma bakin ciki rayuwar nan sai ke, jira nake duk a bar wajen In duba kayan a tsanake" Umma ta bata hannu suka tafa tana dariya, maganganu marasu dadi Umma da kawayenta suka dinga saki a parlorn, Anty da abun ya isheta ganin sai xancen mara lafiya suke tace "Ai kuma Hajiya abun fa ba daga nan yake ba, sai a ga kuma mara lafiya ya samu abun arxiki a rayuwa fiye da mai lafiya, so nawa kuma aka yi hakan" wani dariya Umma tayi tace "Toh ayi mu ga ko basilin xai toya kosai" Anty tace "Kwarai kuwa xai toya sai dai a dau lkci kawai" Hajiya Laraba tace "Toh ni duk wannan abun fa har yanxu ban ga amarya ba" Umma tace "Ohh tana can makaranta, gobe xata taho sun ma kusa gama jarabawa" Hajiya Laraba tace "Ayya tana Zarian kenan" Umma tace "In sha Allah" Mikewa Ammi tayi tace "Toh Hajiya Allah ya sanya alkhairi xan je in ci gaba da abinda nake yi" a dakile Hajiya tace "Oh toh madallah, ban ma san an gayyato ki ba da ina da niyyar tura Ummi ta kira ki sai ga ki" Ammi bata tanka ta ba tana kallon Anty tace "Anty Amina, bari inje in ci gaba da girki, kaya sun yi kyau maa sha Allah, Allah ya sanya alkhairi yasa ayi da mu" Anty tace "Toh ameen Ammi sai na shigo" Mikewa Imaan tayi xata bi Ammi Anty tace "Au har xa ki tafi don gulma" murmushi tayi ta shige gaba, daga Umma har kawayenta suka bi su da kallo ana tabe baki. Sai bayan da suka kusa part dinsu Imaan tace "Ammi yaushe ne bikin?" Ammi tace "Me ya hanaki tambayarsu a can" Imaan bata ce komai ba har suka shiga gidan. Da magrib Imaan taje kai ma Inna abinci taga akwatunan jere a parlonta, Inna tace "Kinga akwatunan yar uwar ki kuwa?" Imaan ta girgixa kai tace "A'a ban ga kayan ciki ba" Inna ta mike ta shiga sakko da su tace "Taho ki fiddo su ki gani, ni sai naga kamar ma mijin rufin asiri kawai garesa, ji fa na yarinyar nan Khadijah guda takwas aka kawo har da gwal biyu a ciki wannan kuwa ko axurfa ban gani ba sai dankunnayen kauye" imaan ta rufe baki xata yi dariya inna ta tabe baki ta xauna tace "Toh naga duk sai saurayin ya wani xo ya cika mana kofar gida da katuwar mota, ga kaya nan kuma duk abun kunya, anya ba gudunmawar da dangi suka dinga basa ya xuxxuba mata a akwatunan ba kuwa, ji fa har da man mai gurguwa na gani a ciki, man da aka yi yayi tun lkcn haihuwar Mujaheed" Imaan ta fashe da dariya har da kyakyatawa, Inna tace "Ni daga ganin dankunnayen da sarakuna dama jikina yyi sanyi, atamfofin kuwa har da na roba guda biyu idan dai ba idona ne yyi min karya ba, ga wani uban lace duk nauyin tsiya, sannan jallabiyoyin irin Wanda na taba siya a makka tun ina goyan Ahmadu da naje, bari in fiddo ki gani, ni da dai a kira min yaron inji muguwar da ta hada ma jikata wannan kayan" tana kokarin fiddo jallabiyar Yusuf ya shigo parlon tare da Mujaheed, Inna ta juya tace "Kun ga kayan yar uwar ku kuwa?" Yusuf yace "Na gani sai dai ko M.A" inna ta mike tace "Toh kai isuhu baka ga irin kayan ba, dama katuwar motar karya yake kawo mana kofar gida ya paka?" Yusuf ya bude baki yana kallonta, ta tabe baki ta xauna ta rungume hannu tace "Ni dai ba ruwana, sai kace xa a basa baxawara" Yusuf yace "Haba inna ina laifinsa duk fa kayan masu tsada ne wllh" a fusace Inna tace "Amma kai dai mugu ne wannan yaro, kai ka yarda ka hada ma figalalliyar budurwar nan ta ka wannan kayan, kai kana ganin idan mun kai masu xa su amsa, mutanen da suka jik'a cikin kudi gidansu gari guda motoci ta ko ina, Kai in takaice maka Idan basu koro mu da kayan ba kace ba ni ba" Imaan ta fashe da wani dariya har da kwanciya inna ta fiddo jalabiyyar ta watsa masu kamar xata yi kuka tace "Ku ji fa kayan da na taba siya lkcn ina goyan ubanku a makka" Ganin dariyar da Imaan take Mujaheed ya daure fuska yana kallonta yace "Ke waye kike ma dariya a nan wai" a fusace Inna tace "A'a bar ta tayi wannan ae abun dariya ne, har da fa mai gurguwa da basilin irin na tale tale, bar min ita tayi dariyarta" Tsaki Mujaheed yyi yace "Toh Allah ya sa ta samu hakan ita" A rikice inna ta mike tace "Auxubillahi... Bakin ka ya tsari danyen kashi Mujaheed, kai ka so a kawo ma Imaan irin wannan tarkacen, ai da na shiga uku wllh, bari kaji duk mai auren Imaan sai ya shirya a duniyar nan, idan na amshi akwatunan ta babu gwal na dan kunne, sarka da awarwaro da zobe kace ba ni bace, sannan atamfa idan na amshi na kasa da dubu ashirin kace ba nice Hajiya patu ba, kai in takaice maka idan ba akwatuna sha biyu ba dama kada shegen da ya xo yace xai aureta don xai ga barbadin bala'i" Mujaheed da ke gyada kai ya tabe baki yace "Ae sai ku yi ta xama, kinga sai ki jik'a ta ki shanye ko kiyi kwadonta ki cinye" daga haka ya fice a parlon, Yusuf ya girgixa kai ya fita shi ma, inna tace "Gantalallu kawai yan hassada wanda basa son ci gaba na, a haka xa ku yi ta gantali a titi." Alhamdulillah, Thanks to all those that patronize the book *Imaan* Allah bar ku da iyayen ku, My book Imaan is for sale coz I am done with free pages tun friday, ni nasan it will go round as usual, I can't prevent that, but if you should come across it it's not for free, i repeat it's not for free, na siyarwa ne, wllh I am too grown up to say Allah ya isa, but have the fear of Allah SWT in u, don't forget it's my property, hakkina ne, wahalata ce, pay before reading, pay before reading, or you just over look it and smile, have a very good conscience plss, and a good conscience won't read happily without paying, if you want any favor pertaining to d book contact me and let me know, the book is 300 via..... Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah 07087865788 and then u contact me through this digit to be added in the payment groups. Thanks once more for patronizing. For those saying xa su same shi a banxa yana yawo to gashi... amma fa ba a banxa yake ba wllh, there is power in the tongue, Karamin hakkin da ka raina..... 😃😃Kasancewar ranan Alhamis ne Imaan na dawowa schl bayan ta yi wanka ta fito ta d'an ci abinci kadan ta koma bedroom ta saka kayanta ta sake fitowa parlor, Ammi dai sai kallonta take don tun daga ganin d'an abincin da ta ci ta san da matsala, Ammi tace "What's wrong with you?" A hankali tace "Ammi cikina xai fara min ciwo ne" Ammi tace "Toh Allah ya sauwake abincin ya ishe ki?" Kai ta gyada mata ta xauna kusa da ita tace "Ammi na dade fa ban je gidan gwaggwo in gaisheta ba" Ammi tace "Jiya ma ta tambaye ki da muka yi waya, ran Saturday idan kin dawo islamiyya sha biyu sai ki tafi, before four ki taho gida saboda islamiyyan yamma" Imaan tace "Toh Ammi me yasa gobe baxan je ba" Ammi tace "A'a xan je xa mu duba ma Halima kaya an kawo daga dubai, idan kin dawo schl ma baxa ki sameni" Imaan tace "Toh, Ammi ankon mu fa?" Ammi tace "Idan kin je sai ki tambayeta" Imaan tace "Ammi bikin na Anty Seeyama xa a fara yi ko Anty Halima?" Ammi tace "Na Seeyama saura two weeks, Halima kuma saura sati hudu" Imaan tace "Toh Ammi na Seeyama baxa a mana anko ba?" Wani kallo Ammi tayi mata tace "Kin ishe ni kuma haka" Shiru Imaan tayi, can ta mike tace "Ammi xan je wajen inna" Ammi tace "Toh sai ki dauko magana idan kika tashi dawowa" dariya kawai tayi ta sa takalminta ta fita parlon ta rufe kofar. Inna na share waje Imaan ta sameta, Inna ta mike tace "Baki ji bayana ba Imaan tun daxu ban xauna ba wllh, aiki dai aiki dai, to kuwa idan mutum bai yi aiki ba ai sai kazanta ta ra6e sa, to ni ko yaushe xan yarda hakan ta faru???" Imaan tace "Toh me kike sharewa a nan din, naga ba datti" inna ta xaro ido tace "Toh k'uran dake yashe a kasa kuma uwaki ce ba datti ba?" Imaan ta yi dariya tace "Toh ai sai kiyi ta sharewa" daga haka ta shiga ta bar ta a wajen, bayan minti goma inna ta shigo parlon ganin yanda Imaan take yatsine yatsine ta hade rai tace "Me kuma ya faru?" A hankali tace "Wllh cikina ne xai fara min ciwo" Inna tace "Toh tashi ki tafi gidan ku ba ruwana da wahalan ki, ko ba jini bane" Imaan tace "Toh ai bai xo ba kawai dai yana min ciwo ne" inna tace "Toh kiyi maxa ki tafi uwar ki ta kai ki asibiti, haka wancan karan kika cuce ni kika daga min hankali, ni dai da xaki dinga rufa min asiri duk kika ji baki da lafiya ki daina taho min nan sai kin ji sauki, a gaskiya kina shiga alhakina" Imaan bata tanka ta ba, Inna tace "Kin ko ji abinda nace" Imaan ta daure fuska tace "Sai nan da kwana biyar ko shidda ma xai xo, ni dama haka yake min ba shi bane" Inna ta tabe baki ta mike ta nufi dakinta tace "Ni dai ba ruwana kar a xo a dameni a gigita ni" Imaan ta gama juye juyenta bacci ya dauketa. wajajen karfe shidda Inna na daki duk ta fiddo da kayan closet dinta tana masu linkin guga jin an bude kofa ta ajiye kayan xata fita parlor, ta labule ta hangi Mujaheed tsaye cikin parlorn, kana ganinsa kasan daga aiki yake don ko tie din wuyarsa bai cire ba kan farar shirt din jikinsa, kallon Imaan dake bacci ya tsaya yi sannan ya kalli kofar dakin Inna, can dai ya karasa kusa da ita ya duka ya kai hannu a hankali kan goshinta yana feeling temperature dinta, sauke hannunsa yyi kan wuyarta ta bude ido tana kallonsa, yace "What's wrong?" Cikinta ta nuna masa kamar xata yi kuka, daga cikin dakin ya ji muryar inna tana cewa "Don Allah a dinga kyakkyawan xato dai, Shikenan ita kuma a rashin lafiya xata kare kamar warce ta kashe mai rai ka wani kai hannu kana tattaba jikinta kaji ko da xafi ko babu, to babu, kuma lafiyar jikata qlau ka matsa wajen tunda fatan ciwo kake mata, dama likitancin hauka ne" Mujaheed ya dinga kallon kofar dakin, inna ta fito tace "A dai ji tsoron Allah a dinga kyakkyawan xato fisabilillahi, lafiyarta lau wllh, al'adarta ce kawai ke kan hanya shine ta langwabe haka, ka shigo kana wani tabe taben jikinta salon a ja mata wani ciwon tunda a haka ake so ta kare" Shi dai kawai tsayawa yyi yana kallon inna fuskarsa daure, can ya juya ya nufi kofa, inna tace "Toh Ina yini... yanxu ka dawo daga aikin kenan" bai tanka ta ba har ya fice parlon. Kafin magrib Imaan ta watsake gaba daya, bata shirya barin part din Inna ba sai kusan karfe goma na dare tare da Yusuf, Inna na kallon Yusuf tace "Isuhu wai daga na fadi ma Mujaheed gaskiya daxu shine har yanxu bai tako nan ba, to me xai bani da Allah bai ban ba, banda ma magana da yake sa ni idan ya xo, ni dai kai da Imaan kun isheni ni kar ma ya sake xuwa" Yusuf yyi murmushi bai dai ce komai ba ya fita yana kallon Imaan dake tsaye gaba daya hankalinta na kan film da ake yace "Ko dai in tafi ne Imaan" tace "A'a ya Yusuf jira ni, ynxu xa a gama" yace "Toh ki kwana nan mana" da sauri ta fice a parlon har tana tuntube, Yusuf ya fara dariya, Inna ta ja tsaki tace "Toh banda ki yamutse min gado ki bar ni da aiki amfanin me xaki min idan kin kwana Imaan?" Yusuf ya kulle mata kofarta suka wuce, a hanya yace "Me yasa baki son kwana wajen inna imaan?" Ta make kafada tace "Karfe uku idan ta tashi sai tasan yanda tayi ta tashi mutum, tayi ta masa surutu har sai baccin ya fita idonsa" Yusuf yyi dariya yace "Dole ma gobe ki kwana can tunda Friday ne" Imaan tace "Sai dai kai ka kwana" daga haka ta shige balcony dinsu tana daga masa hannu yyi murmushi yana kallonta yace "Good night" yana wucewa ta shiga ciki ta kulle kofarsu. "Wannan iskancin da kike ki tafi exams babu karatu baxa ki min shi a gidan nan ba wannan karan" Cewar Ammi kenan tana kashe kayan kallon parlon gaba daya, Imaan ta dinga kallonta kamar xata yi kuka bata dai ce komai ba, Ammi ta nemi waje ta xauna tana danna wayarta, A hankali Imaan tace "Ranan Monday fa ne exams din Ammi, i still have Saturday and Sunday sannan Monday da safe" Ammi tace "Ki tashi ki dau abincin Inna ki kai mata baxa kiyi kallon ba, kuma I promise you har ku gama jarabawan nan baxa ki kunna kayan kallo a gidan nan ba, ko yaushe kika xama dedicated da kallo haka ban sani ba" da mamaki Imaan ke kallonta, can tace "Amma ammi ban taba daukan sama da second position ba fa a schl" Ammi tace "Ur silly First position ba karatu? I want to see ur grade idan kika yi karatu this time around" Imaan ta dauke kai kamar xata yi kuka tace "Ni da ma ba wani kallo nake ba sai lkci lkci kuma da ace 5th nake dauka shine sai ki ce in daina kallo fa Ammi" Ganin kallon da Ammi ke mata ta mike ta sa hularta ta wuce kitchen ta dau abincin inna dake ajiye tun daxu ta fice gidan, har ta isa part din inna ji take kamar ta fashe da kuka, ta bude kofar ta shiga, xaune ta tadda inna da bowl din fura a gabanta ta daura kafa daya kan daya, Yusuf na xaune parlon shi ma da cup din furan a hannunsa, sai Ummi dake shan furan ita ma, Mujaheed dai idonsa na kan tv ga nasa cup din furan a kusa da shi, Inna na ganin Imaan ta daure fuska ta rufe furan gabanta ta mayar bayan ta tace "Ni dai wllh ya kare, ba ruwana sai kun ga mutum da abu ku wani dinga tururuwan xuwa, to duk na rabar..." Imaan ta ajiye abincin hannunta tace "Toh ni ina ruwana da furanki ce maki nayi xan sha?" Inna ta kalli Ummi tace "Ke tashi ki shigar min da abina ciki" Ummi ta mike ta dau furan ta kai daki ta fito, imaan ta turo baki tace "Sai kace nace xan sha" Inna tace "Toh ai sai ki juya ki tafi koh?" Imaan ta ki fita don har ranta take son fura da nonon barin idan inna ce ta dama kuma ita tayi furan da kanta, inna ta kalli na Mujaheed tace "Dama ga wannan Boss din ya ji sha, ko raina wanda na tarfa masa yayi Oho, da yake Rukayya ce tayi min wahalan aikin furan Ahmadu kuma ya siyo min nonon, cewa ma yayi baxai sha ba ki dauka ki sha, Allah yayi da rabon ki" Yusuf yyi yar dariya yana kallon Imaan, Imaan ta saci kallon Mujaheed dake kallon TV har sannan, ta kalli rabin cup din furan kusa da shi, inna tace "Tunda fa aka ji yace baxai sha ba fa baxai sha ba, kawai ki dauka rabon ki ne, don ni bani da wanda xan baki in kwana da yunwa" Imaan tace "Toh wai ni nace maki xan sha ne?" Tana magana tana kallon kofar parlon lkci daya ta suri cup din tayi waje a guje Yusuf ya kyalkyale da dariya don yasan abinda xata yi kenan, Inna ta washe baki tana kallon Mujaheed tace "Allah ya kara" mikewa Mujaheed yyi fuska daure ya bi bayanta, Inna ta rushe da dariya har da kyakyatawa tana kallon Ummi tace "Da dai ki tashi ki kulle min kofa da makulli tunda sun fita" Kafin Imaan ta kai rabin hanya dama gaba daya furan duk ya xube saboda gudun da take, Mujaheed ya cafketa daga karshe ta fasa ihu ta sake cup din hannunta ta kama hannunsa tace "Wayyo Yaya don Allah kayi hakuri inna ce tace in dauka" da mamaki yake kallonta yace "Yaushe na fara wasa da ke gidan nan amma?" Jikinta na rawa tace "Don Allah kayi hakuri Yaya" fuska daure yace "Kiyi providing min furan nan yanxun nan idan ba haka ba wllh kinji na rantse sai na sa ki kuka" ta fashe da kuka amma ba hawaye tace "Yaya bayan kana gani duk ya xube nima ban sha ba, don Allah kayi hakuri xanje waje in siyo maka wllh" ya wani hade fuska yace "Wannan nake so ba na waje ba" ta marairaice tace "Toh yanxu yaya a ina xan samo maka wani, nima fa kaga bata bani ba" ya kalli part din Inna sannan ya kalleta, murya can kasa yace "Kinsan abinda xa ayi yanxu?" Ta kara marairaicewa tana girgixa masa kai, yace "Komawa xa kiyi part dinta ki shiga daki ki fito da bowl din furan da gudu yanda kika fito min da nawa yanxu" ta xaro ido tana kallonsa, sai kuma ta fashe da dariya tace "Yaya kasan baxata bari ba fa" ya hade rai yace "Irin dubaran da kika yi kika fita da nawa haka xaki fito da wancan ma ae" Imaan ta dinga dariya har da kyakyatawa, ya ja kunnenta yace "Baxa ki daina wannan dariyar mahaukatan ba" ta hadiye dariyar da kyar tace "Toh amma tare xa mu sha?" Yace "Eh mana" tana murmushi tace "Toh nasan yanda xan yi" a tare suka koma part din inna ya nuna mata bayan window din bedroom din inna yace "A can xa ki sameni ina jiran ki" tace "Toh" daga haka ya wuce yana waigota, a guje Imaan ta shige parlon inna tana cewa "Wayyo inna kice masa wllh kar ya ta6a ni xan gaya sa da Abba, inna kice kar ya taba ji xan kira daddy na...." Mujaheed yyi murmushi ya koma bayan window din ya tsaya yana shafa kansa, Inna ta mike da sauri kar Imaan ta take ta koma wani wajen ta xauna tace "Fito min daki wllh, ba ruwana ku je can ku karata kar wanda ya dameni, yara dai kamar na jaraba" Imaan da ta shige dakin tuni ta dinga dariya kasa kasa ta dau bowl din furan ta datse murfin yanda idan tana gudu baxai xube ba, ta tattara rigar jikinta tayi saitin bakin kofar fita sannan ta fice a dari da sittin, inna ta kyakkyafta ido don tabbatar da abinda ta gani hannunta amma tuni Imaan har ta fice parlon kamar xata tashi sama, inna ta mike da sauri tace "Isuhu me na gani a hannunta kamar kwanon fura na???" Ummi ta kyalkyale da dariya tace "Wllh shi ne" Yusuf ya fashe da dariya, Inna ta fashe da kuka tana kallonsa. Imaan bata tsaya ba sai da ta isa inda Mujaheed yake jiranta, murmushi yayi ya amshi bowl din yace "Yauwa kinyi kokari" ta washe baki tace "Nagode" ya xauna kan dakali dake wajen ya bude bowl din ya dau ludayin ciki ya juya furan sannan ya fara sha, Imaan ta daina murmushin da take ta durkusa gabansa tace "Yaya kai kadai xaka sha" Ya harareta yace "Toh da ni da wa xa mu sha?" Ta xaro ido tace "Wllh baxan yadda ba ni fa na sha wahala na dakko kaga irin gudun da nayi yanxu ma fa kirjina ciwo yake" banxa yyi da ita yana shan furansa don furan inna ba dai dadi da gardi ba, Ta fashe da kuka tana kallon sa, ya hade rai ya debi rabin ludayin hannunsa ya kai bakinta, ta turo baki tace "Wannan d'an kadan din bayan kai cika wanda xaka sha kake?" Yace "Baxa ki bude bakin ba" ta bude bakin da kyar, ya xuba mata yace "Toh tashi ki tafi" kamar jira take tace "Wllh baxan tafi ba ji fa abinda ka bani bayan ni na sha wahalan daukowa, Allah sai dai ka bani in mayar" Yace "In baki ki gudu da shi gidanku dai" Ta fashe da wani dariya har da kyakyatawa, ya harareta ya ci gaba da shan furan, kamar xata yi kuka tace "Yaya" ya kalleta sannan ya debo furan rabin ludayi ya kai bakinta, kin bude baki tayi tana masa wani kallo, ya kai bakinsa ya shanye, ta fashe da kuka, yayi light murmushi ya kara deba ya kai bakinta, bude bakin tayi ya juye mata, daga nan ya ci gaba da sha bai kara kallonta ba, kiris ya rage ta fashe da kukan gaske, ganin bai san tana yi ba ta fixge ludayin hannunsa, ya wara ido yace "Ke ina wasa da ke ne" ko kallonsa bata yi ba xata diba ganin xai dauke bowl din ta marairaice tace "Don Allah yaya ka bari in sha wllh baxan cika ba" yace "To diba in gani" ta turo baki ta ciko ludayin ta kai baki da sauri, ko shanyewa bata yi ba ya fixge ya juye ragowar a bowl din sannan ya diba ya kai baki, tana ganin haka ta dauke bowl din ta kai baki ta kwankwade ya xaro ido kafin yace komai suka ji muryar Inna cikin kuka tana cewa "Ahmadu idan ba a bi min hakkina ba yau a babbake ni cikin dare idan na kwana cikin gidan nan" Mikewa Mujaheed yyi da sauri xai bar wajen imaan ta mike ta rikosa a rikice tace "Wayyo yaya kai ne kace fa in dauko" Ya wani xaro ido yace "Ni?? You are sick, kar ma ki sa ni a maganan nan" daga haka ya bar gun da sauri don da dukkan alama nan suke taho, Imaan ta bi sa da gudu har suka iso gaban compound din gidan, ya wani hade rai yace "Wai me yasa kike bi na ne ma dai tukun?" Ta marairaice tace "Yaya kai fa ka sa ni" Ya xaro ido yace "Ohh dama idan nace ki shiga wuta sai ki shiga, kar ki kuskura ki ambato sunana a maganan nan" on a serious note ya fadi hakan, ta hararesa tace "Wllh kai ne kace in dauko da gudu in fito" xai yi magana suka ji alamar suna tahowa, inna na cewa "Kuma ko tantama babu wannan tantirin Mujaheed din da ka haifa ne xai sa ta, banda haka imaan ta san wani sace abincin mutane ta fita da gudu, wllh a min iyakan gaske da yaran nan a gidan nan yau, a kan me xa su dinga cutata suna ci min mutunci haka, wai har sun shanye furan sun bar min kwano a bayan window, me nayi masu a rayuwa xa su min haka" tana kai wa nan ta rushe da kuka, Anty tace "Kiyi hakuri don Allah inna" a fusace inna tace "Shegiya nake idan na hakura, a sace min furan a shanye kice in hakura kamar uwata tace min je ki kya gani, ae Aisha dai ta haifi fitina, wannan yarinya Imaan dai fitina ce wllh, a ma kira min Bukar yanxu, idan ban tada gidan nan da bala'i ba yau ace bani ba" da sauri Mujaheed ya nufi gate, imaan kamar xata fashe da kuka tace "Wayyo yaya" sai da ya kusa gate ya juya yana kallonta ya fara dariya kasa kasa, bin bayansa tayi da gudu, gun motarsa dake parke a kofar gida ta gansa xai bude maxaunin driver, ya buda ido yace "Wai me yasa kike bi na ne?" Ta karasa gun motar tace "Wllh yaya ni ba ni kadai xa a gani a gidan ba bayan ni da kai muka shanye, kawai Ammi ta kama ni ta min duka" ya daure fuska yace "Kinga ki juya ki koma ciki wllh" ta fashe da kuka ta make masa kafada, ya shige driver seat, ta bude front seat ta shiga tana turo baki, yace "Wai kin san inda xa ni" kin cewa komai tayi, jin an bude gate ya rufe door dinsa da sauri, Yusuf ne ya fito, Mujaheed ya tada motarsa ya yi zooming off, Yusuf ya dinga dariya mai gadi na kallonsa, sai da suka hau saman titi Mujaheed ya kalleta yace "Dama seriously idan kika kira sunana a case din nan wllh sai na sa ki kukan sati daya, sai ki gaya masu furan ma ke kadai kika shanye" Ta gefen ido ta kallesa kafin tace "Sai dai in ce masu ludayi daya da rabi kawai na sha sauran kuma ban san wanda ya shanye ba" Yace "Kina son in sauke ki nan kenan" ta marairaice tana kallon sa, yace "Toh me xaki fada masu a kan furan" a hankali tace "Cewa xanyi ayi hakuri ni da yaya muka shanye" parking yyi gefen titi, ta rikosa da sauri tace "Aa yi hakuri xan ce ni kadai na shanye" ya hade girar sama da ta kasa yace "Ki rantse" Kamar xata yi kuka tace "Bayan ni da kai muka sha" Alhamdulillah, Thanks to all those that patronize the book *Imaan* Allah bar ku da iyayen ku, My book Imaan is for sale coz I am done with free pages tun friday, ni nasan it will go round as usual, I can't prevent that, but if you should come across it it's not for free, i repeat it's not for free, na siyarwa ne, wllh I am too grown up to say Allah ya isa, but have the fear of Allah SWT in u, don't forget it's my property, hakkina ne, wahalata ce, pay before reading, pay before reading, or you just over look it and smile, have a very good conscience plss, and a good conscience won't read happily without paying, if you want any favor pertaining to d book contact me and let me know, the book is 300 via..... Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah 07087865788 and then u contact me through this digit to be added in the payment groups. Thanks once more for patronizing. For those saying xa su same shi a banxa yana yawo to gashi... amma fa ba a banxa yake ba wllh, there is power in the tongue, Karamin hakkin da ka raina..... 😃😃Gidan wani cin abinci Mujaheed yyi parking, yace "Ki jira in fito..." da sauri tace "Nima ba abinda na ci wllh" ya kashe wayarsa kamar baxae ce komai ba sai kuma yace "meat pie daya ya ishe ki" kafin tace komai ya bude motar xai fita, da sauri tace "Yaya amma fa ban sa takalmi ba" da sauri ya kalli kafarta, yace "Good kinga sai ki jira ni in ci abinci in fito" Ta fashe da kuka tace "Wllh haka xan fito, ni fa ba abinda na ci tun da rana sai furan nan da ka tsammin" ya hade rai yace "Ki fito ki ja min kallo cikin mutane" ta marairaice tace "Yaya to mu je ka siya min ko bathroom slippers ne" yace "Ki dai jira yanxu xan gama cin abincin in fito" Bude motar tayi ta fito, ya xaro ido yana kallonta, Xata xagayo inda yake ya mata tsawa yace "Tsaya nan kar ki xo min nan" ta turo baki tana kallon sa yace "Dama ki tsaya sai na shiga sannan ki shigo, kuma ki nemi can nesa da ni ki xauna xan sa a kai maki abincin can" a hankali tace "Toh" Daga haka ya shiga yana waigota don tabbatar da ta bar distance sosai tsakanin su, Yana xaunawa sai ga ta ta shigo, ya wani hade rai ya dauke kai, tabe baki tayi ta nemi nesa da shi ta xauna ba tare da ta damu da kallon da ake mata cikin eatry din ba, jollof rice da half chicken yasa aka kawo masa da five alive drink sai bottle water, yana kallon waitress din yace "Ae kuna da meat pie koh?" Tace "Ehh har da burger da pizza with sausage roll duk akwai" yace "Good kinga wancan matar dake xaune at that far end?" Waitress din ta kalli inda yake nunawa ganin imaan tace "Ehh na ganta" yace "Ki kai mata meat pie daya da table water, ni xan biya bill din" tace "Ohk" daga haka ta wuce ta dau meat pie din da table water ta nufi gun Imaan tana ajiye mata a gabanta imaan ta kalli Mujaheed da ya dauke kai yana cin abincin gabansa, waitress din ta juya ta wuce, satan kallonta Mujaheed yyi suna hada ido ya juya kujerar sa yayi backing dinta yana murmushi yana cin abincin sa, Imaan ta dinga kallon sa amma ya ki juyowa, bayan kusan minti uku ya sake juyawa a hankali, kawai ganinta yayi a gabansa tana kallon sa kamar xata yi kuka, da sauri ya fara kalle kallen eatry din ya ga kallonsu kawai ake, ya xaro ido kafin yace komai ta ajiye masa meat pie da ruwan a gabansa ta jawo plate din abincin da drink ta dauka ta koma inda take ta xauna ta fara ci, Mujaheed bai ce komai ba ya dauke kansa, bayan kusan minti goma ya mike ya tafi ya biya kudin abincin da snack sannan ya dawo ya dau meat pie din da ruwa yana satan kallonta ita ma kallonsa take, mamaki ya cika sa ganin har ta kusan cinye shinkafar nama kuwa ta ma gama da shi, ya dauke kai ya nufi kofar fita, imaan ta mike da sauri ta dau sauran five alive din ta bi bayansa, a tare suka iso gun motar, ya bude driver seat ya shiga ita ma ta shiga gaba yace "Fita ki koma ki cinye abincin" tayi yar dariya tace "Dama fa nasan wucewa xaka yi ka bar ni shi sa nake ta kallon ka" ya hade rai yace "Fita nace" tace "Ai na koshi baka ga na cinye naman ba" tada motar yayi ya bar eatry din, bayan sun hau saman titi yace "Xan maida ki gida yanxu, wllh kika kuskura kika ce nasan komai a kan furan inna Allah xan sa ki kuka" da mamaki tace "Kai ina xa ka yanxu?" Yace "Gidana" ta fashe da kuka tace "Toh shine ni xaka maida ni gida, wllh kar ma ka kai ni don baxan fita daga motar nan ba" ya buda ido yace "Toh ina xan kai ki?" Ta turo baki tace "Mu tafi gidan ka tare" ya gyada kai yace "Tunda ke mahaukaciya ce ni ba mahaukaci bane" ta kallesa tace "Toh da ba ina xuwa ba" ya jefa mata wani kallo yace "Da ba yanxu bane" Shiru tayi ganin ya dau hanyar gida ta kamo sa tace "Don Allah yaya kar ka maida ni gida yanxu, wllh Ammi xata iya dukana don dama tace kar in dauko mata magana" yace "Toh ina xan kai ki?" Hawaye ta fara yi, yayi murmushi yace "Gobe baxa ki dauke ma tsohuwa furanta ba, ni dama ba ruwana" ta hade kai da gwiwa tana kuka a hankali, bayan few minutes yace "Abinda xai faru yanxu ina maida ki gida sai ki shige dakin Anty da sauri, ki kwana a can" ta dago tana goge hawayen idonta tace "Don Abba ya gani ko, kasan Ummi xata ce ma Abba ina nan" Ya daga kafada yace "Ae shi Abba baxai doke ki ba, fada kuma baya nuna wa a jikin mutum" parking yyi yace "Oya fitar min a mota sai da safe" wasu hawaye na xubo mata ta bude motar ta fita tana kallon sa tace "Duk abinda ya faru daga farko har karshe xan gaya ma Abba baxan boye masa komai ba, tare muka shanye furan kuma kai ka sa na shiga dakin Inna in dauko saboda ta xuba maka kadan" daga haka ta bar wajen da sauri tana kuka ya bi ta da kallo baki bude, tuni ta shige gate ta dinga rabe rabe har ta isa parking space din su Yusuf, a haka har ta shige parlour rufin asirinta ba kowa da gudu ta wuce dakin Anty, Anty dake xaune gaban madubi ta bude baki tana kallonta, Saman gadonta Imaan ta hau ta rufa da duvet, Anty tayi murmushi tace "Ina Mujaheed din?" Imaan ta cire duvet din ta mike xaune kamar xata yi kuka tace "Yace baxai dawo ba yau kuma wllh Anty shi yasa in dauko mata furanta sai ma kinga abinda ya tsammin duk ya shanye sauran" hawaye cike idonta take maganan, Anty tayi dariya tace "Ae ko kun sha jaraba yau, don har yanxu Abba da Ammi na can ana ba Inna hakuri, nima gajiya nayi na taho" Imaan ta turo baki ta koma ta rufe kanta da duvet. Washegari Saturday Imaan na xaune gaban madubin Anty tana shafa mai don har tayi wanka, Anty kuma na xaune kan darduma hannunta rike da hisnul Muslim aka bude kofar dakin, Abba ne tsaye bakin kofar, Imaan ta kusa faduwa saboda rudewa, Abba ya kalli Anty yace "Amina amma baki ce min yarinyar nan na nan ba" Anty tace "Ni ma har na yi bacci na ganta jiya da daddare" Abba ya kalli Imaan yace "Ki sameni parlona yanxu" kamar xata yi kuka tace "Abba to shi yaya fa?" Dakuwa Abba yyi mata yace "Stupid girl, yayan banxa ai duk xa ku gane kuran ku yau" daga haka ya juya ya fita, Imaan ta fashe da kuka tana kallon Anty tace "Kinga ni kadai xa a ma fada yaya ya gudu koh" Anty tace "Ni dai ba kin sani nayi karya ba, maxa fita ki tafi ki samesa ba ruwana" da kyar Imaan ta bar dakin sanye da Hijab dinta, Abba dake parlonsa ya mike ganinta yace "Mu je" bin sa tayi tana goge hawayen idonta suka nufa part din inna, tun daga nesa suka hango Mujaheed yana share mata frontage, Yana ganin Abba ya mike tsaye, Ya gaida Abba da ladabi Abba ya masa banxa ya shiga parlon inna, inna ta fito kitchen tace "Ahmadu ne da sassafe haka" Abba ya xauna ya gaisheta ta amsa, ganin Imaan ta hade rai tace "Ya xaka shigo min da ita parlor Ahmadu, ni da dai ta tsaya daga bakin kofa, tsoronta ma nake ji wllh" Abba ya kalli Imaan yace "Koma can" komawa tayi bakin kofar ta tsaya, Abba yace "Shi yaushe Mujaheed din ya xo nan?" Inna ta xauna tace "Ko minti biyar ba ayi ba, Ashe jiya na shiga alhakin yaron bai ma san me ke faruwa ba baya gidan yana asibiti, sai yanxu da ya shigo nake basa labarin abinda yarinyar ta min, ya taya ni jimami sosai yayi mamaki ainun, shine ya ga xan share waje ya amshi tsintsiyar yake sharewa yanxu duk da dai nasan ba sharuwa wajen xai yi ba amma ai dai ya fi babu" Abba ya sunkuyar da kai yana murmushi, Inna tace "Yanda yarinyar nan ta sa na kwana da yunwa jiya gaskiya Ahmadu idan ba a dau mataki ba xan tafi inje duk inda Allah yayi ko kasar waje ne kuwa, don na gaji da cutata da take, jiya mun dade muna magana da Bukar a waya a kan yarinyar tasa yana ta bani hakuri ni dai ban hakura ba" imaan ta fashe da kuka tace "Wllh yaya ne yasa in dauko masa kwanon furan fa" Abba ya kalli inna da ta bude baki tana kallonta, yace "Ke sai kika yarda da yace maki bai san me ke faruwa ba dama?" A hankali Mujaheed ya ajiye tsintsiyar hannunsa xai bar wajen Abba yace "Don't try that, come in now" Inna ta mike tace "Toh amma ko gaskiya Ahmadu ka haifi abinda ya fi karfin ka, ka haifi tashin duniya, yanxu duk dadin bakin da ya shigo ya min da sa hannunsa a sace min fura da nono, Haba da walakin goro a miya, dama wani Mujaheed ne xai amshi tsintsiya ya min shara, ko da kuwa aiki xai kasheni baxai yi ba wllh, wato xuwa yayi ya yaudare ni ya cuce ni to akwai hisabi ai, ni dama nasan ina imaan ta koyi wani sata idan ba sa ta aka yi ba, ilai ga maganata nan, kuma wllh kaji rantsuwar musulmi ko, to baxan yadda ba sai sun san yanda suka yi aka min furata mai kyau mai kamshi da tsafta irin tawa sannan a siyo min kindirmo mai kyau idan ba haka ba gaskiya abinda xai biyo baya a gidan nan har kai sai ya shafa Ahmadu" Mujaheed ya shigo parlon kansa a kasa, inna na kallonsa da kyau tace "Mugu katon banxa kawai, wllh yau idan na maku Allah ya isa kai da figaggiyar yar nan sai ya bi ku don kun ci da hakkina, ku ka bar ni na kwana da bakar yunwa, to amma ya xanyi, sai dai ku ci albarkacin Ahmadu da Bukar don ni ba abinda na hada da ku, ba dangin iya balle na baba, kawai sai dai ku ci albarka cin 'ya 'yan da na haifa tunda su suka haifo ku duniyar, to banda 6are ma wa xai maka haka, ai 'ya yana baxa su min haka ba, amma kuma Ahmadu ka min iyaka da su kar kato ko figaggiyar da ta sake xuwa bangarena bana bukata Isuhu ya ishe ni rayuwar duniya" Imaan sai hararanta take ta gefen ido, Mujaheed dai kansa na kasa, Abba yace "Toh bana son sake ganin kai ko Imaan a bangaren nan" da sauri Inna tace "Har abada kuwa, don gaskiya idan suka xo sun ja ma kai da Bukar fitina, ita ta tsaya iya bangarensu, shi ma ya tsaya iya nasu, kada wanda ya tsallaka ya yo min nan don xan gudu in bar gidan" Abba yace "Hope u both are apprehending?" Mujaheed yace "In sha Allah" Inna tace " Kuma kafin gobe a kawo min furata da aka yi a kuma siyo min kindirmo nah" Abba yace "Xa su san yanda suka yi in sha Allah" inna ta kalli Imaan tace "Ke kin ma ci halas ya kika kare da ciwace ciwace balle kin dau hakkin mutane, jarababbiya kawai" Imaan ta fashe da kuka Inna tace "Fita can kije ki ma uwar ki Aisha, fitar min a parlor" Juyawa tayi da gudu ta fita tana rusa kuka, Inna ta kalli Mujaheed tace "Kai ma fita, har abada kada ka sake tako min nan, kaje can ka saci furan uwar ka idan ta yi" ta gefen ido ya harareta ya fice a parlon, Abba yace "Ki kara hakuri xan sake ja masu kunne" tace "A'a ni ba ruwana ba dai na gama yanke hukuncin da nake so ba suje can su karata, sai kuma ko wannensu yyi ma uwarsa rashin mutunci ba dai Inna ba" Abba yyi murmushi bai dai ce komai ba. A hanya Mujaheed ya tadda imaan tana kuka bakin rai kamar xata shide, ya tsallake ta yayi wucewarsa. Mujaheed na komawa part dinsu dakin Ummarsa ya nufa, tun da ya shigo take kallonsa ya xauna yace "Ina kwana Umma?" Tace "Ban kwana ba, yanxu duk abinda xaka janyo a xageni a ci min mutunci baka gudunsa ko Mujaheed? Wannan kakar taka wai dole ne sai kaje inda take tunda ita jarababbiya Allah yayi ta, sannan kuma yunwa kake ji da ka dau shegen furanta jiya ta daga mana hankali a gidan nan, ni duk wannan bai wani dameni ba, babban damuwata a nan shine yaushe har ka fara shiri da yarinyar nan Imaan da ku ka dauke furan a tare ku ka sha?" Mujaheed ya bude ido sosai yana kallonta yace "Shiri kuma Umma? Ni bamu wani sha fura tare da ita ba, nine ma na dauke furan na sha" Umma tace "Toh naji tana cewa kai ka tura Imaan daukan furan ku ka raba" ya girgixa kai yace "A'a ba haka bane" Umma tace "Sannan da ake nemanka jiya ina ka tafi, ita yarinyar ma bata gidan a jiya da daddaren" Yace "Ni fa eatry na tafi cin abinci karfe sha daya ya wuce na shigo duk kun yi bacci" tana masa wani kallo tace "Toh ita imaan din ina ta tafi?" Yace "Ban sani ba gaskiya" Umma tace "Mujaheed?" Kallonta yayi tace "Mujaheed?" Yayi Shiru yana dubanta tace "Sau nawa na kira ka?" Ya sauke idonsa kasa tace "Toh wllh idan baka kama kanka gidan nan ba xan sa6a maka, ita kanta innar daga yau na kashe xuwa sashinta, kar ka sake tunda ba kanwar uwata bace ita din, idan kana son gaida kakarka ne sai ka shirya ka tafi katsina uwata na can da ranta" murmushi kawai Mujaheed yyi, tace "Dama tun shekaranjiya akwai maganar da nake son mu yi to da ka dawo gun aiki sai ka tare gun alakakan matar can sai nayi bacci xaka shigo min nan" ya daga kai ya kalleta yace "Toh ina ji Umma" tace "Kasan Hajiya Mansura kuwa?" Ya girgixa kai yace "A'a" tace "Ka santa mana, wata warce ka taba kai ni gidanta a Marafa, ka koma dauko ni da yamma ruwa ya tsuge har tace ka shigo ka ci abinci ka ki ci?" Yace "Ohh na tuna ban san sunanta ba ai" tace "Toh ita ce Hajiya Mansura, dama tana da wata budurwa yar shekara ashirin da daya tana karatu a Malaysia, to ina jin last week suka dawo hutu, baka ganta ba kyakkyawa fara doguwa ga hankali da nutsuwa, shine nake baka shawaran don me baxa ka neme ta ba" Shiru Mujaheed yyi bai ce komai ba, Umma tace "Sunanta Safeena, nasan ma xaka so ta ne coz she have all the qualities, uwa uba ga ubanta mugun attajiri abokin ma d'angote ne aka ce" Murmushi Mujaheed yyi bai dai ce komai ba, Umma tace "Ba batun murmushi bane wannan, dama gashi saura wata hudu ta kare karatun, last week da naje gidan na ganta ta kwanta min har nayi ma Hajiya Mansurar magana ita ma ta ji dadin tunanin nawa don ta yaba da hankalin ka, yanxu abinda nake so da kai ka shirya kaje gidan ko xuwa Sunday tunda baka xuwa aiki da safe, dama xan baka sako ka kai ma Hajiya Masurar nasan xaka ga Safeenar" Murya can kasa Mujaheed yace "Toh, Allah ya kai mu" Umma tace "Ameen son, Allah maka albarka" yace "Ameen, xan je in yi breakfast Umma" tace "Toh shikenan" mikewa yayi ya fita dakin ya kulle mata kofar. Karfe takwas Mujaheed ya fito xai fita kofar gida yaga imaan tsaye jikin mota tana jiran fitowarsu Maimoon su wuce islamiyya, idonta ya kumbura kana ganinta kasan ba karamin kuka ta ci ba, tunda ya fito take kallonsa ta wani cika kiris ya rage ta fashe, Mujaheed ya saci kallonta suna hada ido ya dauke kai, ta fashe da wani matsanancin kuka, da sauri ya kalleta kafin yace komai ta shige gidan da gudu, direct parlon Abba ta nufa, ta samesa kuwa yana kallon news shi kadai, ta xube nan tsakiyar parlon ta dinga rusa kuka kamar xata shide, ya mike da sauri yace "Subhanallah, me ya faru mamana?" Tana kuka sosai tace "Abba Yaya ne ke min dariya, Wayyo Abba" da mamaki yake kallonta, yace "Dariyar me yake maki" ta kara fashewa da kuka tace "Nima ban sani ba wllh Abba" komawa yayi ya xauna yace "Xo nan" mikewa tayi ta koma kusa da shi tana kuka sosai, yayi murmushi ya rungumeta yace "Ya isa haka mamana kiyi hakuri kinji" ta kasa cewa komai yace "To baxa ki daina kukan ba?" Da kyar tace "Xan daina" Ya dau handkerchief ya mika mata yace "Toh goge idon ki kiyi Shiru" tana sauke ajiyar xuciya ta amsa tana goge idonta wasu hawayen na sakkowa, Umma ce ta shigo parlon rike da mug din ruwan Lipton yana turiri, tun da ta shigo take kallon Imaan dake rungume jikin Abba har sannan ta dinga kallonta da wani expression a fuskarta, Umma ta dai ajiye mug din hannunta xata xauna Abba yace "Nemo min Muhammad" Umma tace "Muhammad kuma, lafiya? Ina jin dai ya fita uxurin gabansa ba gwanda a kai ta asibiti ba idan ma ciwon nata ne ya tashi" Abba ya dau wayarsa yayi dialing number Mujaheed, Mujaheed dake xaune gun mai kiosk dake 2 houses away bayan ya siya card ya dinga kallon screen din wayarsa ganin Abba ke kira, ya daga ya kai kunnen kafin yace komai Abba yace "Muhammad ka sameni parlona yanxu" Daga haka ya katse wayar, Umma ta tsaya kallon Abba fuska daure, ba a dau lkci ba Mujaheed ya shigo parlon da sallama, sosai gabansa ya fadi ganin Imaan kusa da Abba ga Umma ma tsaye a parlon, ya sunkuyar da kai ya duka kasa a hankali yace "Abba gani" Abba na kallon Imaan yace "Me kika ce ya maki mamana" cikin rawar murya tace "Dariya ya min ban san ko ya san Ammi ta doke ni bane" Abba yace "Subhanallah ta doke ki kuma, me kika mata" ta fara kuka tace "Wai na sha ma inna fura shine ta mareni ta kuma dokeni a bayana" Abba yace "Aa bata kyauta ba xan je In sameta yanxu kuwa, kai kuma Mujaheed dariyar Uwarka kake mata" Umma ta dinga ma Abba wani irin kallo, Mujaheed ya girgixa kai yace "Abba ni ban fa ganta ba balle in mata dariya" Imaan tace "Wllh ya gan ni ya dinga kallona a sace" tana fadin haka ta fara share hawayen dake sakko mata, Mujaheed yace "To tayi hakuri tunda tace na mata dariya amma ni ban mata ba" Imaan ta turo baki ta dauke kai, Abba yace "Ai kin hakura koh" kin cewa komai tayi Abba yace "Toh kiyi hakuri mamana Aisha kuma zan je in sameta yanxu, maxa tashi ki tafi makarantar kar ki makara" Umma ta fice parlon rai a bace, a hankali Imaan tace "Abba nasan su Maimoon sun tafi yanxu" Abba yace "To mu je in ajiye ki" yana fadin haka ya mike ya dau makullin mota, Mujaheed ya mike yace "Bari in ajiyeta Abba" Abba ya dau dubu biyu ya bata yace "Toh ga kudin lunch din ki" ta rusuna ta amsa. Alhamdulillah, Thanks to all those that patronize the book *Imaan* Allah bar ku da iyayen ku, My book Imaan is for sale coz I am done with free pages tun friday, ni nasan it will go round as usual, I can't prevent that, but if you should come across it it's not for free, i repeat it's not for free, na siyarwa ne, wllh I am too grown up to say Allah ya isa, but have the fear of Allah SWT in u, don't forget it's my property, hakkina ne, wahalata ce, pay before reading, pay before reading, or you just over look it and smile, have a very good conscience plss, and a good conscience won't read happily without paying, if you want any favor pertaining to d book contact me and let me know, the book is 300 via..... Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah 07087865788 and then u contact me through this digit to be added in the payment groups. Thanks once more for patronizing. For those saying xa su same shi a banxa yana yawo to gashi... amma fa ba a banxa yake ba wllh, there is power in the tongue, Karamin hakkin da ka raina..... 😃😃Gidan wani cin abinci Mujaheed yyi parking, yace "Ki jira in fito..." da sauri tace "Nima ba abinda na ci wllh" ya kashe wayarsa kamar baxae ce komai ba sai kuma yace "meat pie daya ya ishe ki" kafin tace komai ya bude motar xai fita, da sauri tace "Yaya amma fa ban sa takalmi ba" da sauri ya kalli kafarta, yace "Good kinga sai ki jira ni in ci abinci in fito" Ta fashe da kuka tace "Wllh haka xan fito, ni fa ba abinda na ci tun da rana sai furan nan da ka tsammin" ya hade rai yace "Ki fito ki ja min kallo cikin mutane" ta marairaice tace "Yaya to mu je ka siya min ko bathroom slippers ne" yace "Ki dai jira yanxu xan gama cin abincin in fito" Bude motar tayi ta fito, ya xaro ido yana kallonta, Xata xagayo inda yake ya mata tsawa yace "Tsaya nan kar ki xo min nan" ta turo baki tana kallon sa yace "Dama ki tsaya sai na shiga sannan ki shigo, kuma ki nemi can nesa da ni ki xauna xan sa a kai maki abincin can" a hankali tace "Toh" Daga haka ya shiga yana waigota don tabbatar da ta bar distance sosai tsakanin su, Yana xaunawa sai ga ta ta shigo, ya wani hade rai ya dauke kai, tabe baki tayi ta nemi nesa da shi ta xauna ba tare da ta damu da kallon da ake mata cikin eatry din ba, jollof rice da half chicken yasa aka kawo masa da five alive drink sai bottle water, yana kallon waitress din yace "Ae kuna da meat pie koh?" Tace "Ehh har da burger da pizza with sausage roll duk akwai" yace "Good kinga wancan matar dake xaune at that far end?" Waitress din ta kalli inda yake nunawa ganin imaan tace "Ehh na ganta" yace "Ki kai mata meat pie daya da table water, ni xan biya bill din" tace "Ohk" daga haka ta wuce ta dau meat pie din da table water ta nufi gun Imaan tana ajiye mata a gabanta imaan ta kalli Mujaheed da ya dauke kai yana cin abincin gabansa, waitress din ta juya ta wuce, satan kallonta Mujaheed yyi suna hada ido ya juya kujerar sa yayi backing dinta yana murmushi yana cin abincin sa, Imaan ta dinga kallon sa amma ya ki juyowa, bayan kusan minti uku ya sake juyawa a hankali, kawai ganinta yayi a gabansa tana kallon sa kamar xata yi kuka, da sauri ya fara kalle kallen eatry din ya ga kallonsu kawai ake, ya xaro ido kafin yace komai ta ajiye masa meat pie da ruwan a gabansa ta jawo plate din abincin da drink ta dauka ta koma inda take ta xauna ta fara ci, Mujaheed bai ce komai ba ya dauke kansa, bayan kusan minti goma ya mike ya tafi ya biya kudin abincin da snack sannan ya dawo ya dau meat pie din da ruwa yana satan kallonta ita ma kallonsa take, mamaki ya cika sa ganin har ta kusan cinye shinkafar nama kuwa ta ma gama da shi, ya dauke kai ya nufi kofar fita, imaan ta mike da sauri ta dau sauran five alive din ta bi bayansa, a tare suka iso gun motar, ya bude driver seat ya shiga ita ma ta shiga gaba yace "Fita ki koma ki cinye abincin" tayi yar dariya tace "Dama fa nasan wucewa xaka yi ka bar ni shi sa nake ta kallon ka" ya hade rai yace "Fita nace" tace "Ai na koshi baka ga na cinye naman ba" tada motar yayi ya bar eatry din, bayan sun hau saman titi yace "Xan maida ki gida yanxu, wllh kika kuskura kika ce nasan komai a kan furan inna Allah xan sa ki kuka" da mamaki tace "Kai ina xa ka yanxu?" Yace "Gidana" ta fashe da kuka tace "Toh shine ni xaka maida ni gida, wllh kar ma ka kai ni don baxan fita daga motar nan ba" ya buda ido yace "Toh ina xan kai ki?" Ta turo baki tace "Mu tafi gidan ka tare" ya gyada kai yace "Tunda ke mahaukaciya ce ni ba mahaukaci bane" ta kallesa tace "Toh da ba ina xuwa ba" ya jefa mata wani kallo yace "Da ba yanxu bane" Shiru tayi ganin ya dau hanyar gida ta kamo sa tace "Don Allah yaya kar ka maida ni gida yanxu, wllh Ammi xata iya dukana don dama tace kar in dauko mata magana" yace "Toh ina xan kai ki?" Hawaye ta fara yi, yayi murmushi yace "Gobe baxa ki dauke ma tsohuwa furanta ba, ni dama ba ruwana" ta hade kai da gwiwa tana kuka a hankali, bayan few minutes yace "Abinda xai faru yanxu ina maida ki gida sai ki shige dakin Anty da sauri, ki kwana a can" ta dago tana goge hawayen idonta tace "Don Abba ya gani ko, kasan Ummi xata ce ma Abba ina nan" Ya daga kafada yace "Ae shi Abba baxai doke ki ba, fada kuma baya nuna wa a jikin mutum" parking yyi yace "Oya fitar min a mota sai da safe" wasu hawaye na xubo mata ta bude motar ta fita tana kallon sa tace "Duk abinda ya faru daga farko har karshe xan gaya ma Abba baxan boye masa komai ba, tare muka shanye furan kuma kai ka sa na shiga dakin Inna in dauko saboda ta xuba maka kadan" daga haka ta bar wajen da sauri tana kuka ya bi ta da kallo baki bude, tuni ta shige gate ta dinga rabe rabe har ta isa parking space din su Yusuf, a haka har ta shige parlour rufin asirinta ba kowa da gudu ta wuce dakin Anty, Anty dake xaune gaban madubi ta bude baki tana kallonta, Saman gadonta Imaan ta hau ta rufa da duvet, Anty tayi murmushi tace "Ina Mujaheed din?" Imaan ta cire duvet din ta mike xaune kamar xata yi kuka tace "Yace baxai dawo ba yau kuma wllh Anty shi yasa in dauko mata furanta sai ma kinga abinda ya tsammin duk ya shanye sauran" hawaye cike idonta take maganan, Anty tayi dariya tace "Ae ko kun sha jaraba yau, don har yanxu Abba da Ammi na can ana ba Inna hakuri, nima gajiya nayi na taho" Imaan ta turo baki ta koma ta rufe kanta da duvet. Washegari Saturday Imaan na xaune gaban madubin Anty tana shafa mai don har tayi wanka, Anty kuma na xaune kan darduma hannunta rike da hisnul Muslim aka bude kofar dakin, Abba ne tsaye bakin kofar, Imaan ta kusa faduwa saboda rudewa, Abba ya kalli Anty yace "Amina amma baki ce min yarinyar nan na nan ba" Anty tace "Ni ma har na yi bacci na ganta jiya da daddare" Abba ya kalli Imaan yace "Ki sameni parlona yanxu" kamar xata yi kuka tace "Abba to shi yaya fa?" Dakuwa Abba yyi mata yace "Stupid girl, yayan banxa ai duk xa ku gane kuran ku yau" daga haka ya juya ya fita, Imaan ta fashe da kuka tana kallon Anty tace "Kinga ni kadai xa a ma fada yaya ya gudu koh" Anty tace "Ni dai ba kin sani nayi karya ba, maxa fita ki tafi ki samesa ba ruwana" da kyar Imaan ta bar dakin sanye da Hijab dinta, Abba dake parlonsa ya mike ganinta yace "Mu je" bin sa tayi tana goge hawayen idonta suka nufa part din inna, tun daga nesa suka hango Mujaheed yana share mata frontage, Yana ganin Abba ya mike tsaye, Ya gaida Abba da ladabi Abba ya masa banxa ya shiga parlon inna, inna ta fito kitchen tace "Ahmadu ne da sassafe haka" Abba ya xauna ya gaisheta ta amsa, ganin Imaan ta hade rai tace "Ya xaka shigo min da ita parlor Ahmadu, ni da dai ta tsaya daga bakin kofa, tsoronta ma nake ji wllh" Abba ya kalli Imaan yace "Koma can" komawa tayi bakin kofar ta tsaya, Abba yace "Shi yaushe Mujaheed din ya xo nan?" Inna ta xauna tace "Ko minti biyar ba ayi ba, Ashe jiya na shiga alhakin yaron bai ma san me ke faruwa ba baya gidan yana asibiti, sai yanxu da ya shigo nake basa labarin abinda yarinyar ta min, ya taya ni jimami sosai yayi mamaki ainun, shine ya ga xan share waje ya amshi tsintsiyar yake sharewa yanxu duk da dai nasan ba sharuwa wajen xai yi ba amma ai dai ya fi babu" Abba ya sunkuyar da kai yana murmushi, Inna tace "Yanda yarinyar nan ta sa na kwana da yunwa jiya gaskiya Ahmadu idan ba a dau mataki ba xan tafi inje duk inda Allah yayi ko kasar waje ne kuwa, don na gaji da cutata da take, jiya mun dade muna magana da Bukar a waya a kan yarinyar tasa yana ta bani hakuri ni dai ban hakura ba" imaan ta fashe da kuka tace "Wllh yaya ne yasa in dauko masa kwanon furan fa" Abba ya kalli inna da ta bude baki tana kallonta, yace "Ke sai kika yarda da yace maki bai san me ke faruwa ba dama?" A hankali Mujaheed ya ajiye tsintsiyar hannunsa xai bar wajen Abba yace "Don't try that, come in now" Inna ta mike tace "Toh amma ko gaskiya Ahmadu ka haifi abinda ya fi karfin ka, ka haifi tashin duniya, yanxu duk dadin bakin da ya shigo ya min da sa hannunsa a sace min fura da nono, Haba da walakin goro a miya, dama wani Mujaheed ne xai amshi tsintsiya ya min shara, ko da kuwa aiki xai kasheni baxai yi ba wllh, wato xuwa yayi ya yaudare ni ya cuce ni to akwai hisabi ai, ni dama nasan ina imaan ta koyi wani sata idan ba sa ta aka yi ba, ilai ga maganata nan, kuma wllh kaji rantsuwar musulmi ko, to baxan yadda ba sai sun san yanda suka yi aka min furata mai kyau mai kamshi da tsafta irin tawa sannan a siyo min kindirmo mai kyau idan ba haka ba gaskiya abinda xai biyo baya a gidan nan har kai sai ya shafa Ahmadu" Mujaheed ya shigo parlon kansa a kasa, inna na kallonsa da kyau tace "Mugu katon banxa kawai, wllh yau idan na maku Allah ya isa kai da figaggiyar yar nan sai ya bi ku don kun ci da hakkina, ku ka bar ni na kwana da bakar yunwa, to amma ya xanyi, sai dai ku ci albarkacin Ahmadu da Bukar don ni ba abinda na hada da ku, ba dangin iya balle na baba, kawai sai dai ku ci albarka cin 'ya 'yan da na haifa tunda su suka haifo ku duniyar, to banda 6are ma wa xai maka haka, ai 'ya yana baxa su min haka ba, amma kuma Ahmadu ka min iyaka da su kar kato ko figaggiyar da ta sake xuwa bangarena bana bukata Isuhu ya ishe ni rayuwar duniya" Imaan sai hararanta take ta gefen ido, Mujaheed dai kansa na kasa, Abba yace "Toh bana son sake ganin kai ko Imaan a bangaren nan" da sauri Inna tace "Har abada kuwa, don gaskiya idan suka xo sun ja ma kai da Bukar fitina, ita ta tsaya iya bangarensu, shi ma ya tsaya iya nasu, kada wanda ya tsallaka ya yo min nan don xan gudu in bar gidan" Abba yace "Hope u both are apprehending?" Mujaheed yace "In sha Allah" Inna tace " Kuma kafin gobe a kawo min furata da aka yi a kuma siyo min kindirmo nah" Abba yace "Xa su san yanda suka yi in sha Allah" inna ta kalli Imaan tace "Ke kin ma ci halas ya kika kare da ciwace ciwace balle kin dau hakkin mutane, jarababbiya kawai" Imaan ta fashe da kuka Inna tace "Fita can kije ki ma uwar ki Aisha, fitar min a parlor" Juyawa tayi da gudu ta fita tana rusa kuka, Inna ta kalli Mujaheed tace "Kai ma fita, har abada kada ka sake tako min nan, kaje can ka saci furan uwar ka idan ta yi" ta gefen ido ya harareta ya fice a parlon, Abba yace "Ki kara hakuri xan sake ja masu kunne" tace "A'a ni ba ruwana ba dai na gama yanke hukuncin da nake so ba suje can su karata, sai kuma ko wannensu yyi ma uwarsa rashin mutunci ba dai Inna ba" Abba yyi murmushi bai dai ce komai ba. A hanya Mujaheed ya tadda imaan tana kuka bakin rai kamar xata shide, ya tsallake ta yayi wucewarsa. Mujaheed na komawa part dinsu dakin Ummarsa ya nufa, tun da ya shigo take kallonsa ya xauna yace "Ina kwana Umma?" Tace "Ban kwana ba, yanxu duk abinda xaka janyo a xageni a ci min mutunci baka gudunsa ko Mujaheed? Wannan kakar taka wai dole ne sai kaje inda take tunda ita jarababbiya Allah yayi ta, sannan kuma yunwa kake ji da ka dau shegen furanta jiya ta daga mana hankali a gidan nan, ni duk wannan bai wani dameni ba, babban damuwata a nan shine yaushe har ka fara shiri da yarinyar nan Imaan da ku ka dauke furan a tare ku ka sha?" Mujaheed ya bude ido sosai yana kallonta yace "Shiri kuma Umma? Ni bamu wani sha fura tare da ita ba, nine ma na dauke furan na sha" Umma tace "Toh naji tana cewa kai ka tura Imaan daukan furan ku ka raba" ya girgixa kai yace "A'a ba haka bane" Umma tace "Sannan da ake nemanka jiya ina ka tafi, ita yarinyar ma bata gidan a jiya da daddaren" Yace "Ni fa eatry na tafi cin abinci karfe sha daya ya wuce na shigo duk kun yi bacci" tana masa wani kallo tace "Toh ita imaan din ina ta tafi?" Yace "Ban sani ba gaskiya" Umma tace "Mujaheed?" Kallonta yayi tace "Mujaheed?" Yayi Shiru yana dubanta tace "Sau nawa na kira ka?" Ya sauke idonsa kasa tace "Toh wllh idan baka kama kanka gidan nan ba xan sa6a maka, ita kanta innar daga yau na kashe xuwa sashinta, kar ka sake tunda ba kanwar uwata bace ita din, idan kana son gaida kakarka ne sai ka shirya ka tafi katsina uwata na can da ranta" murmushi kawai Mujaheed yyi, tace "Dama tun shekaranjiya akwai maganar da nake son mu yi to da ka dawo gun aiki sai ka tare gun alakakan matar can sai nayi bacci xaka shigo min nan" ya daga kai ya kalleta yace "Toh ina ji Umma" tace "Kasan Hajiya Mansura kuwa?" Ya girgixa kai yace "A'a" tace "Ka santa mana, wata warce ka taba kai ni gidanta a Marafa, ka koma dauko ni da yamma ruwa ya tsuge har tace ka shigo ka ci abinci ka ki ci?" Yace "Ohh na tuna ban san sunanta ba ai" tace "Toh ita ce Hajiya Mansura, dama tana da wata budurwa yar shekara ashirin da daya tana karatu a Malaysia, to ina jin last week suka dawo hutu, baka ganta ba kyakkyawa fara doguwa ga hankali da nutsuwa, shine nake baka shawaran don me baxa ka neme ta ba" Shiru Mujaheed yyi bai ce komai ba, Umma tace "Sunanta Safeena, nasan ma xaka so ta ne coz she have all the qualities, uwa uba ga ubanta mugun attajiri abokin ma d'angote ne aka ce" Murmushi Mujaheed yyi bai dai ce komai ba, Umma tace "Ba batun murmushi bane wannan, dama gashi saura wata hudu ta kare karatun, last week da naje gidan na ganta ta kwanta min har nayi ma Hajiya Mansurar magana ita ma ta ji dadin tunanin nawa don ta yaba da hankalin ka, yanxu abinda nake so da kai ka shirya kaje gidan ko xuwa Sunday tunda baka xuwa aiki da safe, dama xan baka sako ka kai ma Hajiya Masurar nasan xaka ga Safeenar" Murya can kasa Mujaheed yace "Toh, Allah ya kai mu" Umma tace "Ameen son, Allah maka albarka" yace "Ameen, xan je in yi breakfast Umma" tace "Toh shikenan" mikewa yayi ya fita dakin ya kulle mata kofar. Karfe takwas Mujaheed ya fito xai fita kofar gida yaga imaan tsaye jikin mota tana jiran fitowarsu Maimoon su wuce islamiyya, idonta ya kumbura kana ganinta kasan ba karamin kuka ta ci ba, tunda ya fito take kallonsa ta wani cika kiris ya rage ta fashe, Mujaheed ya saci kallonta suna hada ido ya dauke kai, ta fashe da wani matsanancin kuka, da sauri ya kalleta kafin yace komai ta shige gidan da gudu, direct parlon Abba ta nufa, ta samesa kuwa yana kallon news shi kadai, ta xube nan tsakiyar parlon ta dinga rusa kuka kamar xata shide, ya mike da sauri yace "Subhanallah, me ya faru mamana?" Tana kuka sosai tace "Abba Yaya ne ke min dariya, Wayyo Abba" da mamaki yake kallonta, yace "Dariyar me yake maki" ta kara fashewa da kuka tace "Nima ban sani ba wllh Abba" komawa yayi ya xauna yace "Xo nan" mikewa tayi ta koma kusa da shi tana kuka sosai, yayi murmushi ya rungumeta yace "Ya isa haka mamana kiyi hakuri kinji" ta kasa cewa komai yace "To baxa ki daina kukan ba?" Da kyar tace "Xan daina" Ya dau handkerchief ya mika mata yace "Toh goge idon ki kiyi Shiru" tana sauke ajiyar xuciya ta amsa tana goge idonta wasu hawayen na sakkowa, Umma ce ta shigo parlon rike da mug din ruwan Lipton yana turiri, tun da ta shigo take kallon Imaan dake rungume jikin Abba har sannan ta dinga kallonta da wani expression a fuskarta, Umma ta dai ajiye mug din hannunta xata xauna Abba yace "Nemo min Muhammad" Umma tace "Muhammad kuma, lafiya? Ina jin dai ya fita uxurin gabansa ba gwanda a kai ta asibiti ba idan ma ciwon nata ne ya tashi" Abba ya dau wayarsa yayi dialing number Mujaheed, Mujaheed dake xaune gun mai kiosk dake 2 houses away bayan ya siya card ya dinga kallon screen din wayarsa ganin Abba ke kira, ya daga ya kai kunnen kafin yace komai Abba yace "Muhammad ka sameni parlona yanxu" Daga haka ya katse wayar, Umma ta tsaya kallon Abba fuska daure, ba a dau lkci ba Mujaheed ya shigo parlon da sallama, sosai gabansa ya fadi ganin Imaan kusa da Abba ga Umma ma tsaye a parlon, ya sunkuyar da kai ya duka kasa a hankali yace "Abba gani" Abba na kallon Imaan yace "Me kika ce ya maki mamana" cikin rawar murya tace "Dariya ya min ban san ko ya san Ammi ta doke ni bane" Abba yace "Subhanallah ta doke ki kuma, me kika mata" ta fara kuka tace "Wai na sha ma inna fura shine ta mareni ta kuma dokeni a bayana" Abba yace "Aa bata kyauta ba xan je In sameta yanxu kuwa, kai kuma Mujaheed dariyar Uwarka kake mata" Umma ta dinga ma Abba wani irin kallo, Mujaheed ya girgixa kai yace "Abba ni ban fa ganta ba balle in mata dariya" Imaan tace "Wllh ya gan ni ya dinga kallona a sace" tana fadin haka ta fara share hawayen dake sakko mata, Mujaheed yace "To tayi hakuri tunda tace na mata dariya amma ni ban mata ba" Imaan ta turo baki ta dauke kai, Abba yace "Ai kin hakura koh" kin cewa komai tayi Abba yace "Toh kiyi hakuri mamana Aisha kuma zan je in sameta yanxu, maxa tashi ki tafi makarantar kar ki makara" Umma ta fice parlon rai a bace, a hankali Imaan tace "Abba nasan su Maimoon sun tafi yanxu" Abba yace "To mu je in ajiye ki" yana fadin haka ya mike ya dau makullin mota, Mujaheed ya mike yace "Bari in ajiyeta Abba" Abba ya dau dubu biyu ya bata yace "Toh ga kudin lunch din ki" ta rusuna ta amsa.A hankali Imaan tace "Abba nasan idan muka fita kilan xai min fada a hanya" Mujaheed ya kalleta bai ce komai ba Abba yace "Toh ya maki fadan mu ga" Murmushi kawai Mujaheed yayi ya fita parlon, Abba yace "Maxa ku tafi kar kiyi latti mamana" Imaan ta bi bayan Mujaheed tana share idonta, tunda Mujaheed ya fito parlon Abba gabansa ya dinga faduwa, xaune ya ga Umma a main parlor fuskar nan nata a tamke, Mujaheed ya karasa inda take, ita ko bata fasa kallonsa ba, kofar fita Imaan ta nufa, Mujaheed yyi kasa da murya yace "Umma dama Abba...." Katse sa tayi tace "Bana son jin komai, Ban baka izinin fita parlon nan ba in har ni na haife ka Mujaheed, ko da kuwa me xai faru yau" Kallonta Mujaheed ya tsaya yi ba tare da yace komai ba, Anty ta fito kitchen da breakfast a hannunta tayi wani dariya tace "Su haihuwa manya...." Umma ta kalleta ta dakatar da ita da sauri tace "Ke in kina cin k'asa ki kiyayi ta shuri, ki daina min shisshigi a lamari na, ki yi mai fissheki kawai a gidan nan" Anty ta tabe baki tace "Anya akwai wanda ya kai me shiga lamarin d'a da ubansa shisshigi kuwa, kuma naga duk wanda xai ce d'a kada ya bi umarnin mahaifinsa shine mai babban shisshigi a rayuwa kuma bai dauko abinda xai fishshesa ba" Umma ta mike rai bace tace "D'an ki ko nawa? tunda ba wata shegiya ce ta haifa min d'an ba sai kiyi ta kanki ki, ki kuma cire min ido kan d'a na" Anty tace "Na wuce in tsaya ina xance irin na yara da ke, amma bari in baki shawara, domin kin haifi Muhammad ba yana nufin ke kadai ke da iko da shi ba duk ki bi ki takura ma yaro sai abinda kike so xai yi a gidan nan, kina amfani da advantage din ganin yana maki biyayya dari bisa dari...." Cikin tsawa Umma tace "Da ke da shawarar taki Allah kwashe maku albarka..." Dai dai nan Abba ya fito parlon jin hayaniya, ya kalli Mujaheed dake tsaye, ya kalli Yusuf dake tsaye stairs yana kallon su shi ma sannan ya kalli su Umma yace "Me ke faruwa nan?" Rai bace Umma tace "Ka ja ma matar ka kunne Alhaji ta fita harkata kada abu ya bace tsakanin ni da ita a gidan nan, ta cire ido kan d'a na, ta kuma yi ta kanta..." Abba ya dakatar da ita yace "I asked what happened kina min warning madam" Anty ta tabe baki tace "D'an ta da ka aika yanxu... ta hana shi xuwa saboda isa da gadara, to ni kuma bana gani inyi shiru...." Abba ya kalli Mujaheed da ya kasa dagowa ya mika masa hannu yace "Bani makullin motar...." Da kyar Mujaheed ya dago yana kallonsa sannan ya kalli Umma, ta watsa masa wani kallo alamar ya basa, a hankali Mujaheed yace "Abba ai bance fa baxan je ba" yace "Eh baka ce ba, amma ba ni" Mika masa makullin Mujaheed yayi, Abba ya kalli Yusuf yace "Here, ka tafi ka ajiye Imaan a makaranta" Yusuf ya karasa saukowa stairs da yake tsaye ya amshi makullin sannan ya nufi kofa ya fita, Juyawa Abba yyi ya koma parlonsa, Mujaheed ya wuce sama a sanyaye, Anty ta tabe baki ta wuce saman ita ma, wani ajiyar xuciya Umma ta sauke ta koma ta xauna ranta fess. Sai bayan da suka bar gidan Imaan ta kalli Yusuf tace "Ya Yusuf Umma ce tace yaya kar ya kai ni koh?" Yusuf na driving yyi murmushi yace "Toh dama ya xa ayi ta bari ya kai ki?? salon ku je ya d'an rankwashe ki ki dawo kina mana ihu kina kuka" xaro ido Imaan tayi tana kallonsa, Ya ki kallonta sai murmushi yake, ta hade rai tace "Toh an doki mutum kuma baxai yi kuka ba" Yusuf yace "A'a xai yi kuka abunsa" Turo baki tayi bata ce komai ba, shi ma bai kuma cewa komai ba har ya iso islamiyyarsu ya tsaya bakin gate, ya kalleta yace "Kin fa yi latti sosai" tace "Ae xa su ga idona kuma cewa xanyi bani da lafiya, dama ban da lafiyan" daga haka ta bude motar ta fita, D'aga masa hannu tayi, yayi mata murmushi ta shiga cikin makarantar. Imaan na dawowa islamiyya karfe sha biyu kashegari lahadi ta fara shirin tafiya gidan gwaggonta wato Mahaifiyar Ammi dake unguwar rimi, Tun da ta fito daki Ammi dake xaune parlor ke kallonta, tsadadden atamfa ne jikinta sai dan kunnenta na gwal, babu abinda ke fuskarta banda eye pencil da chappete da ta goga a lips, sosai tayi kyau duk da haka, da mamaki Ammi tace "Ina xa ki?" Imaan ta xauna kusa da ita tace "Gidan Gwaggwo mana Ammi" Ammi ta mata wani kallo tace "Kin gaya ma Daddy ne?" Ta marairaice tace "Daddy baxai hanani ba fa na sani" Ammi tace "Baxa fa ki fita gidan nan ba sai da saninsa don ba ruwana" tashi Imaan tayi kamar xata yi kuka ta shiga dakinta kiran Abba, wayarta da bata damuwa da ta dauko ta yi dialing number sa, bayan wani lkci ya dauka, ta amsa sallamarsa sannan ta gaishesa, yace "Ya kike Imaan" tace "Lafiya Daddy ya aiki?" Yace "Alhmdllh, har kun dawo islamiyyar?" Tace "Ehh daddy dama gidan gwaggwo nake son in je in gaisheta shine Ammi tace sai na gaya maka" yace "Ae kina da islamiyya da yamma mamana" kamar xata yi kuka tace "Ae kafin karfe hudu xan dawo" yayi shiru kafin yace "Toh waye xai kai ki?" Tace "Ni kadai Daddy ai ina xuwa ni kadai" yace "Kai ma Ammin ta ki waya" fita dakin tayi ta kai ma Ammi waya, Ammi ta amsa ta kai kunne, daddy yace "Why not drop her plss bana son tana fita ita kadai" Ammi tace "Sai kace wata yar shekara goma yallabai, she do go out her self...." Daddy yace "Toh minti nawa ne kin ajiyeta ki dawo" Ammi tace "I told u for the past two month ban shiga motar nan ba, sai dai ta bari next week mu je tare idan Allah ya yarda, ina da aikin da xan yi yanxu, ko jiya fa naje gidan gobe ma xan je, yau kuma sai na kai Imaan?" Daddy yace "Bata wayar" Ammi ta mika mata, daddy yace "Mamana ki bari next week ku je da Ammin ki idan Allah ya kai mu" imaan ta fashe da kuka tace "Bayan na shirya daddy, na fa san hanya ba yau xan fara xuwa ni kadai ba" Daddy ya dan yi shiru kafin yace "Shikenan to kije, but go with ur nose mask, and inhaler, Allah ya kiyaye hanya" tana goge idonta a hankali tace "Toh daddy na gode" Ammi ta shiga kitchen ta dauko dambun naman da tayi ma mahaifiyarta tace "Ki kai ma gwagggo ina gaisheta sai na xo goben" Imaan ta amsa tace "Toh" dubu Biyu Ammi ta bata ta bar gidan bayan tasa gogaggen Hijab dinta har kasa, a dai daita Imaan ta samu da xai kai ta har gidan, bayan sun isa ta sauka ta basa kudinsa sannan ta shiga gate din gidan, babban gida ne sosai da su Ammi suka siya ma mahaifiyar tasu, Ammi ce ta biyu gun gwaggwo bayan babban yayansu Umar, sai maxa biyu da mace daya Anty Murja, duk sun yi aure da 'ya yansu, yar Anty Murja ta biyu Halima ce ke gaban gwaggwo kuma ita xa ayi aurenta kwanan nan, Sosai Gwaggwo tayi murnar ganin Imaan, duk cikin jikokinta ko da bata nunawa ta fi jin Imaan har ranta, Imaan ta rungumeta cike da jin dadin ganinta ita ma, Gwaggwo tace "Kin guje ni Fatima" Imaan tace "Toh Gwaggwo kinga idan naje boko da safe da yamma muna dawowa xan wuce islamiyya, ranan asabar kuma islamiyya safe da yamma, yau ma kawai dai na taho ne kuma da wuri xan koma saboda islamiyya" Gwaggwo tace "Toh Allah ya maki albarka ya baki sa'a a karatun ki, ya Ammin ki fa?" Imaan tace "Tana gaishe ku, tace in kawo maku wannan" Gwaggwo tace "Toh nagode Allah mata albarka, fatan mutan gidanku duk suna lafiya" Imaan tace "Duk lafiya lau" Ammi tace "Mujaheed ya daina xuwa min kwata kwata yanxu yana kasar kuwa?" Imaan tace "Yana nan" Gwaggwo tace "Ikon Allah, shi kuma d'an farin fa, duk da shi baya ma gaida mutane dama" Imaan tayi dariya tace "Shi ma yana nan" Gwaggwo tace "Toh Allah maku albarka, in ji kakarku tana lafiya" Imaan ta turo baki tace "Ehh" Gwaggwo tace "Toh Allah ya kara mana lafiya, ki dauko lemo fridge ki sha" Imaan ta gyara xamanta tace "Anty Halima bata nan ne?" Gwaggwo tace "Taje kai anko" Imaan tace "Toh ni ba a ban ankon ba" Gwaggwo tace "Xa ta kai maki naki har gida tace" Imaan ta washe baki tace "Toh" mikewa tayi ta dauko malt daya ta dawo ta xauna ta fara sha tana cin dambun naman da ta kawo, Gwaggwo tace "Inji yanxu ciwon ki yana sauki sosai kamar yanda mahaifiyar ki ke gaya min idan na tambaya" Imaan tace "Ehh da sauki" Da damuwa Gwaggwo tace "Allah ubangiji ya yaye maki wannan cutar Fatima, in sha Allah xaki samu lafiya gaba daya muna nan muna gaya ma Allah" Yar dariya Imaan tayi tace "Gwaggo ya Salim yana xuwa?" Gwaggwo tace "Yauwa kwanaki yayanki Muhsin ya kawo min karar ki wai baki gaida mutane" Imaan ta hade rai ta daina cin naman da take tace "Ni kullum sai yace bana gaishesa, to ma a ina nake ganinsa balle in gaishesa" Gwaggwo tace "A'a Fatima ga wannan dai waya da ta kawo komai da sauki, ko shi kika dauka ai xa ki kirasa ku gaisa" Imaan ta turo baki tace "Toh shi ma fa ba kulani yake ba wllh" cike da damuwa Gwaggwo tace "Ni dai ku rike xumunci don Allah, ba kya ganin yanda iyayenku ke yi ne, ubansa ya sha nono ya bar ma uwarki, wllh baki da yan uwan da ya wuce su don mutan gidanku ba son ke da uwar ki suke ba duk an sa maku ido, ga kakarku fitinanna, kiyi ma kanki fada ki rike xumunci da yan uwanki na nan, duk suka xo gaisheni sai sun tambayeni ke ba Usman ba, ba Muhsin din ba, ba Salim ba ga matan su ma gaba daya, ke sai kiyi shekara baki xo nan ba baki je gidajen nasu ba shi sa bakwa hadu duk da ba laifin ki bane laifin uwar ki ce don ita ya kamata ta sa ki a hanya ta kuma sa maki ido" Imaan dai sai cin namanta take tana shan malt, sallama aka yi bakin kofa Gwaggwo ta amsa Muhsin ya shigo tare da abokinsa, Gwaggwo tace "Sannun ku da xuwa, yanxu nake xancen ka Muhsin" Muhsin yayi murmushi yana kallon Imaan da ta ki kallonsa yace "Wannan fitsararriyar ce ta xo ashe" Gwaggwo tayi dariya tana kallon abokinsa tace "Sannu da xuwa Sadeeq kwana biyu ka gujeni" murmushi yyi ya cire glass din idonsa ya karaso Inda take ya durkusa yana kallon Imaan da taki dago kai sai cin namanta take yace "Sannu Kaka ina yini" Imaan ta daga kai don muryar sounds soo familiar, Gwaggwo tace "Lafiya lau Sadeeq ya mutan gidanku? Ya kuma aiki da kujuba kujuban rayuwa" ya sauke kansa kasa yace "Alhmdllh mun gode Allah Kaka" Gwaggwo tace "Toh Allah yayi maku albarka ya kare ku sharrin makiya, ya tsare ku da tsarewarsa" a hankali yace "Ameen" ya kai idonsa kan Imaan that was so uncomfortable, Muhsin yace "Ina yini Anty Imaan" boye fuskarta tayi da kujera yace "Ke yanxu kin girma kin daina kula kowa kin mance lkcn da kike kuka sai an goya ki, kiyi ta bamu wahala muna goya ki a anguwa koh" kamar xata yi kuka tace "Ya Muhsin bana so ni yaushe nake kuka a goya ni" yayi dariya yace "Tunda kin girma kin manta ai shikenan, gashi nan ma kin daina gaida kowa" kamar xata yi kuka tace "Ya Muhsin kai ma fa ba magana kake min ba, ni da bani da lafiya ka tambayi Ammi ma, kuma ni ina dadewa ban hau whatsapp ba, wayar ma ba amfani nake son yi da shi ba" yace "Yaushe ne baki da lafiya?" Gwaggwo tace "Kai ma dai Muhsin sai kace baka san dawan garin ba, sai kayi mata addua da fatan samun lafiya" Muhsin yace "Toh Allah ya sauwake Imaan amma ai kina shan magani koh?" Ta gyada masa kai ba tare da ta dago ba, yace "Sannu lil sis" ta turo baki a hankali ba tare da ta dago ba still tace "Ina yini" ya xaro ido yace "Toh boye fuskar ta meye, Kunyata kika fara ji ko na abokina" ya fadi haka yana muna sadeeq dake kallonta, kin dagowa tayi ta kuma ki cewa komai, shi dai Sadeeq sai kallonta yake, Gwaggwo tayi dariya tace "Fatima kenan, to tashi ki shiga ciki" kamar jira take ta mike ta wuce dakin Gwaggwo da sauri, Muhsin yayi murmushi yace "Imaan Daru" mikewa Gwaggwo tayi ta dauko ma Sadeeq ruwa da lemo yace "Da kin bar shi Gwaggwo daga gida mu ke ai" Gwaggwo tace "A'a idan baka son inyi fushi to ka sha, ga dambun nama yanxu Imaan ta kawo min" murmushi yyi ya dau bottle wata daya ya bude, Muhsin yace "Wai ban ga Amaryar gidan nan ba?" Gwaggwo tace "Taje kai anko, nasan tana hanyar dawowa yanxu" Muhsin yace "Da alama dai duk Halima ta kagu ta bar ki" Gwaggwo tace "Don bata nan shine xaka mata wannan sharrin, to bari dai ta dawo" Muhsin yyi dariya yace "A'a ni dai ba ruwana rufa min asiri Gwaggwo" Sadeeq dai sai murmushi yake yana danna wayarsa, hira suka dinga yi gaba daya a parlon har kusan Asr, Muhsin yace "Gwaggwo bari mu je masallaci mu dawo yanxu" Gwaggwo tace "Toh Allah maku albarka" Muhsin ya mike tare da Sadeeq suka nufi kofa, tashi Gwaggwo tayi tana kiran Imaan da bacci ya dauke tun daxu a dakin. Suna fita compound Sadeeq na kallon Muhsin yace "Wacece yarinyar nan Muhsin?" Muhsin ya wara ido yace "Ko dai kana ciki ne Abubakir?" Sadeeq yace "Na santa ne shi sa nake tambayarka" Da mamaki Muhsin yace "Haba, amma ban ga ta nuna alamar ta san ka ba" Murmushi Sadeeq yyi yana shafa sajensa yace "Ni na nuna alamar na santa banda yanxu da na fito?" Muhsin yace "Toh ina ka santa?" Sadeeq yace "Baka fada min relation dinka da ita ba" Muhsin yace "Cousin dita ce, mum dinta ita ce immediate sister din Abbana" da mamaki Sadeeq ke kallon sa yace "You mean you two are this close?" Muhsin yace "Sure" Sadeeq yace "That's Amazing, she is Mariya's school friend kaga dalilin da ya sa na santa" Muhsin yace "Maa sha Allah, amma bata gane ka ba ko?" Murmushi Sadeeq yayi yana maida glass dinsa yace "Ta gane ni sarai, that was why she was uncomfortable" Muhsin yyi dariya yace "Ohh I see, there is something a kasa kenan" Sadeeq yace "Let not miss jam'i plss" daga haka suka shiga masallacin don yin alwala. Imaan na idar da sllh tace ma Gwaggwo xata wuce don xata islamiyya, Gwaggwo tace "Baxa ki ci abincin ba kenan, shinkafa ce da miya fa" Imaan tace "Bana jin yunwa fa Gwaggwo" Gwaggwo tace "Toh shikenan ki duba siff a daki xaki ga wani sabon hijab da na dinka maki da takalmi ki dauka," Imaan tace "In ji me hannu ne Hijab din?" Gwaggwo tace "Ae nasan me hannu kike sawa, shi nayi maki" Bude kofar parlon aka yi Muhsin ya shigo tare da Sadeeq, Muhsin yace "Har kin fito kenan yan matan Ammi" Imaan tayi murmushi tace "Ehh wucewa xan yi saboda islamiyya" Muhsin yace "Mu ma yanxu xa mu wuce ai" Gwaggwo tace "Toh sai ku ajiye min ita don Allah a gida kar ta kara bin k'uran nan ta koma a samu matsala" Dariya Muhsin yayi yace "Wa yaga imaan baturiya" Imaan ta boye fuskarta, dubu biyar Sadeeq ya ajiye ma Gwaggwo yace "To kaka xa mu koma sai wani lkcn kuma, ba yawa wannan ki siya goro" Gwaggwo tace "A'a gaskiya ka dau kayan ka Sadeeq, matsalata da kai kenan idan ka xo gidan nan kai baka gajiya ne" murmushi kawai yayi, Muhsin yace "Shikenan dama ban fito da kudi ba ya fanshe ni, sai ki raba, nawa da nasa" Gwaggwo tayi dariya tace "Allah sarki, Toh Allah dai ya maku albarka ya ba ku mata na gari kuyi aure ku bar xaman nan da ku ke" Muhsin yace "Toh Ameen Gwaggwo" Tare Imaan suka fita da Muhsin don Sadeeq har ya fita, ta bude back seat ta xauna, Sadeeq ne xaune driver seat din Muhsin ya shiga front seat suka bar anguwar. Hira suka ta yi a motar, ita dai danna wayarta kawai take, amma da ta daga kai xa su hada ido da Sdeeq ta madubi, sai tayi maxa ta sauke kanta, bayan tafiyar kusan minti sha biyar ta ji Muhsin yace "Ajiye ni nan man" parking Sadeeq yyi, Muhsin ya fita yana kallonta yace "Toh anmata sai mun yi waya ki gaida Ammi, abokina xai ajiye ki gida" ta xaro ido tace "Ya Muhsin nima nan fa sauka xan yi dama" Muhsin yace "Inaaa... bayan amana Gwaggwo ta ba mu mu kai ki gida kada kura ya taba ki, nima akwai abinda xan yi anguwar nan ne amma da tare xa mu tafi" Imaan ta dinga kallon sa kamar xata yi kuka, ya daga mata hannu yana danne dariyarsa yace "Sadeeq drive her carefully plss sai mun yi waya" daga haka Sadeeq ya ja motar suka hau saman titi, Imaan dai sai wasa take da fingers dinta, bayan wani lkci ta dago a hankali tana kallon gaba suka hada ido ta madubi, da sauri ta sunkuyar da kanta, yayi murmushi yace "Kina tsoron kada in sace ki ko?" Kin cewa komai tayi, bayan kusan minti biyu taji cikin cool voice dinsa yace "I am Abubakar Sadeeq Ahmad, was born and bred up here in Kaduna, first son of the family, my primary and secondary education all in Kaduna, before I proceed to UK where I had my degree and msc, I am a medical practitioner....." Kallon sa kawai Imaan take ta madubi, yyi murmushi yace "Mariya is my step sis, I have six siblings altogether, ranan kinje gidanmu amma part din stepmum dita, namu part din yana cikin gidan though very far away, soo you've known almost all about me... Yes I am still single and searching..." daga haka yyi shiru ya kalleta yana murmushi yace "Do you mind telling me about ur self" shiru tayi da farko, can a hankali tace "Sunana Fatima Abubakar amma ana kirana Imaan" ta kallesa don a hankali yake driving din kasancewar bbu motoci sosai titin, ya gyada mata kai alamar yana ji, yana murmushi, murya can kasa tace "I am the only child of my parent" Da mamaki ya dinga kallonta, ta sunkuyar da kanta tace "I am In the same class with Mariya both School and Islamiyya, muna xaune tare da Daddy na da Ammi, with my paternal grandmum, and my Uncle with his family, i mean my father's senior brother" Sadeeq ya gyada kai a hankali yace "That's nyc, Allah maki albarka ya sa ki xamo the Apple of ur parent eyes" Murmushi tayi murya can kasa tace "Ameen" ganin sai tafiya yake ta bude manyan idonta tace "To ai baka san inda xaka kai ni ba" ya kalleta ta madubi yace "Kin manta ranan da Antynmu ta sa na ajiye ki gida kenan?" Ta wara ido tace "ohh na tuna" ya d'an yi murmushi, suna kusa layin yace "Toh baki fada min samarin ki nawa ba?" Ta xaro ido tace "Samari kuma?" Yace "Yeah" tace "Tabb, ni bani da Samari" yace "Sai dai frnds kenan" ta turo baki, yayi murmushi yana kallonta, tace "A school bani da male frnds, a islamiyya ma haka, a gida ne kawai" yace "Toh su waye?" Tace "Cousins dina" yace "Really?" Ta gyada masa kai, yace "Can I know them" murmushi tayi tace "Ya Yusuf ne sai yaya.. Ohh yaya yusuf ne ma kadai, mun daina shiri da yaya yanxu" yace "Can I know the Yusuf?" Tace "Yea he is my cousin, an engineer yana aiki a nan yana yi a Kano yana yi a zaria" yana parking kofar gidan su yace "Shi dayan fa?" Tace "Yaya?" Ya gyada mata kai tace "Shi wani lkcn yana Abuja wani lkcn yana nan, yanxu yana nan" Sadeeq yace "Maa sha Allah, to me yasa bakwa shiri?" Tace "Yanxu ya fiye mugunta baya kuma kulani kamar da" tana magana ta bude kofar motar tace "Nagode" ba karamin daure ransa yyi ba yace "Wait ara min fone naki pls, I want to confirm ko Muhsin ya tafi da nawa cos I can't find it here" komawa tayi ta xauna ta basa wayarta ya amsa ya gama danne dannensa sai ga ring din wayarsa, ya mayar mata yace "ohhh thanks yana nan ashe" ta fita motar tace "Thanks" yayi murmushin da ya bayana dimples dinsa yace "You are welcm" Xaune ta ga Mujaheed gun mai kiosk a kofar gidan yana kallonta, duk da yanda gabanta ya fadi ta dauke kai da sauri ta wuce cikin gida ta rufe gate. *I want to use this medium to bring this to the notice of my Fans, akwai wani namiji mai amfani da information dina gaba daya both Facebook and WhatsApp, a lot suna chatting da shi a tunaninsu ni ce, to bani bace ba wllh, masu nemana Facebook idan sun yi searching xa su ga account biyu iri daya, to ni nawa account din daga followers kadai ma mutum xai gane it's real me bcos the followers are much, idan mutum ya duba post na timeline dina ma xai gane account dina ne, duk da ko wani update nayi shi ma sai ya sata yayi, ga lambarsa kamar haka masu chatting da shi ta WhatsApp 09031263639.... Billah namiji ne kuyi ta kanku, har card wasu na tura masa da sunan xa su siya littafin Imaan to bani bace, da yawa na cewa sun biya Noor Hayat ban sa su group ba ban basu littafi ba to shi suka ba kudinsu ba ni ba. Beware fans katon namiji ne yake claiming khaleesat Haiydar kuma ni na bar sa da fitowar rana da faduwarsa, duk da ban ma yarda shi din Muslmi bane, Allah ya Isar min, a yanda ya fara a gantale haka xai kare a gantale* Littafin Imaan is 300 via... Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah Show ur evidence of payment through my WhatsApp digit... 07087865788, subscribe and read happily without feeling any guilt. _Su ma masu editing min novel su sa abinda ban yi niyyar sawa ba, bayan fitar da shi da suke ban yi complain ba... we shall meet in the hereafter in sha Allah_ 😇Mikewa Mujaheed yyi ya bi bayanta, tunda Imaan ta shiga gidan daman take waigen kar ya biyo ta, ido hudu suka yi da Umma da ta fito tare da wata bakuwa, ta dauke kai ta ci gaba da tafiyarta da sauri, Mujaheed na ganin Umma dama ya canxa direction dinsa, Umma na kallon sa tace "Daga ina kake?" Yace "Ina xaune a waje, xan wuce wajen aiki ne yanxu" Umma ta bi Imaan da kallo sannan ta kara kallon sa, ya d'an buda ido yace "Umma ni ban gane kallon nan ba, ki tambayi mai kiosk din can tun daxu nake wajen a xaune wllh" Kawar Umma tace "Yi wucewan ka kaji Muhammad" Murmushi Mujaheed yyi ya wuce ciki, tafiya suka ci gaba da yi Umma tace "Gani nayi kamar tare suke da warcan mai laluran da ta wuce yanxu" Hajiya Saude tace "A'a da xan shigo daxu fa na gansa xaune inda yace maki, to minti na nawa a ciki ko minti sha biyar fa ban yi ba" Umma ta sauke wani ajiyar xuciya tace "Da kin san irin k'i da tsanar da nake ma uwar yarinyar nan har cikin raina ko Hajiya Balaraba, wllh abun ba kyau, xan iya komai a duniya don ganin na walakantata, yanda nake jin tsanarta a rai ko kishiyata Amina ban jin ta haka, sai in ki cutar Amina amma ita xan iya cutar ta, sai ga tsanar har ya shafi wannan figaggiya irin ciwon da ta haifo duniya, duk na tsane su kamar yanda na tsani mutuwata, bayan na dawo gidan nan da kyar fa na raba Mujaheed da yarinyar, sai da na tashi tsaye kyamm" Hajiya Balaraba tace "Ikon Allah to sonta yake shi din?" Umma tace "Auzubillahi kaji wata magana wai so, ni na haifi Mujaheed na san halinsa, wllh ba so bane kawai shakuwa ce tsantsa da shisshige masu da yake, sannan yarinyar ta yi mugun sabo da shi, kuma a da kafin in dawo shi ke tsaye kan bata magunguna da dai abubuwa da ya shafi lalurorinta, kin san sickler ce sosai...." Hajiya Balaraba tayi dariya tace "Ba fa a shaidar d'an yau Hajiya, ke kin shiga xuciyarsa ne kika ga ba sonta yake ba?" Umma tayi wani murmushi tace "Kin san akwai wani abokinsa Ibrahim iyayensa hamshakan masu kudi ne, shi ma yaron ya jike jagab da naira, da ban yi da gaske ba wllh ita Imaan din ya so hadawa da yaron wai ya nemeta, ga yaron mai hankali da nutsuwa, wllh sai da na masa jan ido sosai, don in dai ina raye abun arxiki baxai taba xuwa inda Aisha da 'yar ta suke ba, baxan bari ba in sha Allah ina nan ina sa ido in ga wanda xai jajibe yarinyar da gwara babu da ita, kullum fa ana hanyar asibiti kamar 'yar da aka sama ta mugun hanya, to fa da nayi da gaske da Mujaheed shine ya hada yaron da kanwarsa Ummi, yanxu ana gama bikin Seeyama xa a fara xancen na Ummin, Uban yaron fa abokin gwamnan garin nan ne na kut da kut" Hajiya Balaraba tace "Toh Allah dai ya kyauta" Umma tace "Sannan shi Mujaheed din akwai wata yar talakawa da yake mutuwar so wai farida, ni a bincike na ma cewa aka yi idan ban tashi tsaye ba wllh sai ya aureta don yayi mugun kwallafa rai a kanta, baki ga hidimar da yake mata da iyayenta ba, duk ya talike a kansu har haya na samu labarin yana biya masu don nasa mutane su sa masa ido a anguwar, in sha Allah na kusa cire masa yarinyar a ransa gaba daya sai dai idan ba ni ce na haifesa ba, sa'anninsa na neman 'ya yan masu kudi shi ya buge da neman talauci salon su mallake min shi su tsiyace shi, iyayen fa matsiyata ne na gaske wllh" Hajiya Balaraba tace "Toh shi ina ya samota?" Umma tace "Wllh wai ya dawo daga Abuja ranan, kin san wani lkcn jirgin kasa yake biyowa ta a nan anguwar ya ganta dai dai layinsu wai xata Unguwar sanusi, shine fa ya rage mata hanya daga nan kuma ta makale masa ina jin, ni dai ina nan ina kokarin cireta a ransa gaba daya" Hajiya Balaraba tace "Gaskiya kam, Allah dai ya mana tsari" Umma tace "Ameen" sallama suka yi Umma ta koma ciki. Bude kofa Imaan tayi ta fito misalin karfe tara na dare don kwashe socks da kananun kayan da Ammi ta wanke mata a cloth line, da kyar take tafiya don ji take kamar xaxxabi xai rufeta ga ciwon kai, tun bayan Isha Mujaheed ke xaune kan farin kujera ta wajen parking space dinsu, yana jin fitowarta kuwa ya mike ya tsaya kusa da wani flower dake opposite cloth line din, bbu wuta gaba daya a wajen hakan ya ba Imaan mamaki sai tayi tunanin mutuwa bulb din yayi, nan ko shi ya cire bayan ya dawo masallaci, sai da ya jira ta fara kwashe kayan nata sannan ya cafkota ta baya, yasan next action dinta hakan yasa ya rufe bakinta da sauri, tayi mugun tsorata wanda hakan yasa ta fara numfashi da sauri, yayi freeing bakinta yana kallonta don gaba daya ya ma mance da laluran nata, ya dukar da ita da sauri yace "Ke relax now, nine fa, stay still and relax" kasa yin hakan tayi babu bata lkci kuma Asthma dinta ya tashi a wajen, daga ta yayi ya shiga apartment dinsu da ita, Ammi ta mike tana kallonsu, ya xaunar da ita kasa, Ammi ta wuce dakinta ta dauko inhaler dinta ta mika masa ya amsa ya bude cap din ya kai mata baki, sai da Ammi ta ga numfashinta ya fara dawowa steady sannan ta juya ta wuce bedroom dinta. Kwanciya Imaan ke son yi ya dagota yana kallonta yace "Ina ke maki ciwo" Hawaye cike idonta ta nuna masa kafarta, yace "Kin sha magani?" Ta girgixa masa kai, yace "Ina magungunan?" Ta nuna masa bedroom dinta, dagata yayi suka wuce dakin nata, ya dau magungunan ya bude su sannan ya fita xuwa kitchen ya dauko ruwan gora da glass cup ya koma dakin, bata maganin yayi ta karba ta sha, ya mike ya dauko na tube da take shafawa a kafanta da bayanta, dawowa yayi kan gadon ya durkusa kusa da ita ya daga rigar baccin jikinta xuwa thigh dinta, ta bude ido tana kallonsa, duk ta wani langwabe tana sauke numfashi a hankali, shafa mata man xafin ya shiga yi, kamar xata yi kuka murya can kasa tace "Wayyo Yaya yana min ciwo" hararanta yyi bai dai ce komai ba, ta runtse ido ta kama hannunsa tace "Ni wllh ciwo yake min ka min a hankali" Buge mata hannun yyi ta janye da sauri, haka ta dinga yarfe hannu har ya shafe mata maganin daga thigh har fararen toes dinta, gaba daya jikinta ya dau xafi wanda at anytime xaxxabi zae iya rufeta, a hankali tace "Yaya saura bayan" yana kulle tube din yace "Baxan yi ba" da kyar ta mike xaune ta sauke rigan jikinta xuwa waist dinta ta koma tayi rub da ciki, yace "Ki shafa da kanki baxan shafa ba" a hankali tace "Baxan iya ba ae, don Allah ka shafa min" da kamar baxai shafa ba sai kuma ya bude tube din ya matso methylated cream din ya fara shafa mata a bayan a hankali, lumshe ido tayi cikin sanyin murya tace "Yaya kai na ciwo yake min sosai, kamar xaxxabi xan yi" ya hade rai yace "Ina kika tafi daxu?" Ta bude ido da sauri tace "Gidan Gwaggwo naje" yace "Waye ya ajiye ki a mota?" Ta xaro ido sai kuma ta turo baki bata san duk yana kallonta ba, yace "Ba tambayar ki nake ba" kamar xata yi kuka murya can ciki tace "Ya Muhsin ne fa" mintsilinta yyi a bayanta yace "Ni xa ki ma karya?" Ta yi wani kara ta mike xaune da sauri tana shafa wajen, ganin kallon da yake mata ta xaro ido tayi wani karan ta koma tayi rub da ciki tace "Wayyo bana so yaya" yace "Nace wa ya ajiye ki daxu?" Ta rufe idonta tace "Ya Muhsin" yace "You are still lying koh? Wannan yayi kama da motar Muhsin?" Ta turo baki tace "Ya canxa mota" yace "Ohk, idan kika bari na fita dakin nan baki gaya min ko waye ba, this case will pend har ki gama langwabe langwaben ki kuma I promise i will deal with you" kamar xata yi kuka tace "Yaya abokin ya Muhsin ne fa, tare muke da shi sai ya sauka a wani anguwa xai yi wani abu shine abokin ya ajiye ni shi, ka kira ya Muhsin din ma ka tambayesa wllh" yana gyada kai yace "ke yanxu kin girma baki da aiki sai shiga motar karti suna ajiye ki kofar gida koh?" kallonsa take kamar xata fashe da kuka ya mike ya ajiye tube din xai fita, a hankali tace "Yaya baka gama shafawa ba" wani shegen kallo ya mata ya fice dakin. A stairs ya hadu da Umma xata sauko parlor, ya jira ta wuce tana kallonsa tace "Mura kake nake jin kamshin aboniki?" Ya wara ido yace "Oh, eh daxu naji kamar xan yi muran shine fa na shafa a kirji" Umma tace "Toh Allah ya sauwake" daga haka ta wuce shi ma ya wuce sama ya shiga dakinsa, gun injections dinsa ya nufa ya dau pcm da syringe yasa a aljihunsa sannan ya sakko parlor, Umma tace "Ga fa abincin ka can ka bari yana galallawa a dinning" Mujaheed yace "Ohk xan ci Umma" tace "Yanxu ina xa ka?" Yace "Card xan amso waje" daga haka ya fita, sanin halin Ummar tasa, hakan yasa ya fita gidan gaba daya, bayan kusan minti bakwai ya dawo ciki ya nufi part din su Imaan, Ammi na kitchen tana wanke wanke jin an bude kofar parlor ta leko suna hada ido yace "Allura na dauka na pcm naga tana xaxxabi" yana magana yana ciro alluran a aljihu Ammi bata tanka sa ba ta koma kitchen Bedroom dinta ya bude ya shiga ya sameta yanda ya bar ta har ta fara bacci, ya isa kusa da ita ya xauna bakin gadon ya fara hada alluran yana gamawa ya juya yana kallonta yace "Kee" tayi nisa baccin dama gata mai nauyin bacci, sanin haka ya ja hancinta yace "Imaan" bude ido tayi da kyar xata kara rufe idon yace "Baxa ki tashi ba?" A hankali tace "Yaya me xan yi kuma" Ta bude ido sosai ganin abinda ke hannunsa ta mike xaune da sauri tana jan rigar ta xuwa chest dinta tace "Yaya wa xaka ma alluran?" Yace "Gado" kamar xata yi kuka tace "Ka mance na sha magani ne" yace "Kar ki bata min lkci my frnd" ta fashe da kuka tace "Na shiga uku Ammi ni ban ce a min allura ba" Tana fadin haka xata mike ya fixgota ya kwantar da ita ya daga rigar jikinta ya mata alluran ya mike ya fice daga dakin, sai da Ammi ta shigo dakin tana mata mugun kallo sannan ta hakura da kukan ta koma ta kwanta nan da nan kuma bacci ya dauketa. Imaan na dawowa schl ranan litinin taga calls har biyu da ta yi missing, bayan ta idar da sllh tana xaune kan darduman ta dau wayar tayi dialing number din, har ya katse ba a dauka ba, few seconds later sai ga call din ya shigo wayarta, dagawa tayi ta kai kunne, sallama aka yi daga daya bangaren cikin cool voice, tayi shiru da farko, can kuma tace "Waye ne?" Yace "Baki amsa sallama ne?" Tace "Not a must in amsa a fili, who are you" yayi murmushi yace "Ohk then, how are you?" Tace "I asked who are you first?" Yace "Tsoro kike ji?" Tace "Sorry i think it's a wrong call" yace "Why do you say so?" Tace "Because without any doubt I know it's only my dad, mum.... and very few dat have my contact" yace "Ohk... Muhsin ya sa in kira in ji ko kin shiga gida lafiya" ta d'an bude ido da mamaki amma ta kasa cewa komai, yyi murmushi a hankali yace "How are you Imaan?" Murya can kasa tace "Alhmdllh" yace "I guess yanxu kika dawo schl?" Tace "Sure" yace "Alryt, sai islamiyya ko?" Tace "Eh" yace "Ohk then Allah ya kiyaye hanya, amma tare xa ku yi sauka da su Mariya?" Tace "In sha Allah" yace "Saura wata nawa?" Tace "Two months" yace "Maa sha Allah, we will talk later kar kiyi latti" tace "Sai anjima" daga haka ta katse wayar ta mike ta fara shirin Islamiyya. Bayan Magrib Mujaheed na xaune parlon Abbansa da duk yan gidan, Yusuf ma dake xaune wayarsa kawai yake ta dannawa a parlon, Anty duk ta fiddo ankon bikin Seeyama suna nuna ma Abba, Umma dai na xaune ta hade rai don gani take kamar Anty shishshigi kawai take mata, Anty tace "Toh Abba ga kaya nan, gaba daya kala uku ne" Mujaheed yace "Toh duka kala ukun xa su yi?" Anty tace "Ehh ko kana da damuwa da hakan??" murmushi yyi bai ce komai ba, Yusuf ya daga kai yace "Amma fa Anty yayi yawa sai kace su ne..." Mugun kallon da mahaifiyar tasa tayi masa yasa yyi shiru ya ci gaba da danna wayarsa, Abba yace "Kice expenses ne ba na wasa ba, to da wanne ku ke son mutum ya ji, ina laifin ma kala biyu?" Umma tace "Haba Alhaji, abu dai na rana daya lkci daya, ni fa da cewa ma nayi kala hudu hudu Amina tace a bar shi a kala uku kawai" Abba ya gyada kai bai dai ce komai ba, Anty tace "Idan ma baxa ka siya masu ba ga yayyinsu sai su masu" Umma tace "Atoh dai" Yusuf yace "Mu dai sai dai muyi masu kala bibbiyu" Anty tace "Toh ka rike kudin ka" Dariya yayi yace "Shikenan ni sai in ma Rahma da Ummi M.A yayi maku sannan yayi ma Maimoon" Umma tace "Sai kayi ma Kakarku ko kala biyu ne ita ma, shikenan it's settled" Yusuf ya dinga kallon Umma bai ce komai ba, Abba yace "Toh mamana fa?" Anty ta buda ido tace "Ai kuwa Imaan... kaga na ma mance wllh, shikenan sai Mujaheed yayi mata kaga hakan ma is settled" Abba yace "Ehh sai Mujaheed yayi mata" Umma ta yi ma Anty wani kallo tace "Wani Mujaheed din, shi Yusuf me ya hanasa yi mata?" Anty tace "Saboda kince yayi ma Kakarsu, kinga Mujaheed sai yayi ma Imaan" A fusace Umma tace "Toh an ruguje wannan tsarin kowa tayi ma 'yar ta, Inna kuma Alhaji ko baban ita Imaan din su yi mata" Abba yace "Ba tsarin da ya ruguje Hajiya, Mujaheed yayi ma ke, Amina... da maimoon sai Imaan, Yusuf kuma yayi ma Ummi, Rahma da Inna, kuma a cire ma imaan nata a kai mata yanxun nan" Anty ta cire ma Imaan kala uku, Abba ya kalli Mujaheed yace "Dauka ka kai mata" Mujaheed ya kalli Umma da ranta idan yayi dubu a lkcn ya baci, Anty tace "A'a jira, yi min transfer din kudin Imaan din yanxu tukun, sauran ko daga baya ne sai ka yi" Mujaheed ya kasa cewa komai, Anty tace "Malam ka min shiru ina maka magana m" ya dau wayarsa gabansa na faduwa sai dai bai yadda ya kalli Umma da ko ba a fada masa ba yasan kallonsa take, ya gama danne dannensa yace "Anty ina jin ba network...." Ta mike ta isa kusa da shi ta amshi wayar tace "Baxa ka raina min hankali ba" sanin Gtb yake amfani da lkci daya ta danna transfer code dinsu tayi komai ta sa har account number dinta bayan ta sa amount sannan ta mika masa tace "Sa min pin" Karba yyi ya sa pin din ta amshe wayar, duk ya kasa kallon Umma, sai da Anty ta ga transfer din yayi sannan ta basa wayarsa ta koma ta xauna, lkci daya aka turo masa debit ya bude ya ga 30k ta yi transfer, Abba yace "Toh ka dau kayan ka kai mata sai kace mata kai ka siya mata" Kasa tashi yayi, Abba ya hade rai yace "Are you stupid ina maka magana kana xaune, wato abinda kake nufi shine baka jin maganar kowa gidan nan sai na uwar ka koh, ina fa lura da kai kuma nake sharewa" Tashi Mujaheed yayi ya dau ledan kayan ya nufi kofa, Umma ta mike fuu ta wuce sama, Anty tayi wani murmushi a ranta tace "da sauki ai tunda ba bin sa xa ki yi ba" A hankali Mujaheed ya murda kofar apartment dinsu Imaan ya shiga da sallama murya can kasa, Imaan ce durkushe parlon da yar ves sai skirt iya cinya, nose mask na hancinta tana goge gogen kayan da ke daukan k'ura a parlon, ta mike ta cire abun bakinta tana kallonsa, Ammi ta fito parlor jin an shigo, yyi kasa da kai ya ajiye ledan hannunsa kan kujera yace "Abba yace a kawo mata" daga haka ya juya ya fita ya kulle kofar, Imaan xata bude ledan Ammi ta mata tsawa, dakatawa tayi da sauri, fuska daure Ammi tace "Kina ganin ya shigo amma kika ki wucewa daki da wannan shegun kayan jikin ki koh, tun daxu nake maki magana ki nemi kayan arxiki ki sa ko don saboda ciwon ki sannan kada wani ya fado amma kin maida ni mahaukaciya, ke kam wace irin yarinya ce Allah ya bani, in ji hankalin ki ya kwanta da ya shigo ya ganki a haka?" Imaan sai kallonta take da mamaki tace "Ammi yaya ne fa" Bude baki Ammi tayi tana kallonta, can tace "Sai aka yi ya don shi ne?" Tace "Toh Ammi shi ne fa ba wani ba ya shigo, dama dai ya Yusuf ne kin san baxan tsaya haka ba" Ammi ta kasa daina mata kallon mamaki tace "Shi yayan muharramin ki ne Imaan?" Imaan ta xaro ido tace "Ammi yaya fa har wanka ya taba min ina karama, kuma da ba shi ke sa min kaya ba ma idan ban sa ba, ni dai bana jin kunyarsa wllh, dama dai yaya Yusuf ne shi ko dankwali bana tsaya kusa da shi ban sa ba, shi kuma yaya ni xan ma iya cire kaya a gabansa, toh har yau ba yana shafa min magani a kafana da bayana ba, ko wajen inna idan yana nan ina....." Ammi taga bude baki fa ba nata bane ta dau daya daga pillows na kujera ta jefa mata a mugun fusace tace "Ban taba sanin ke shahararriyar mahaukaciya bace sai yau, wato iskanci yasa kike cewa ya shafa maki maganin xafi koh, to in sake gani sai na ci uban ku ke da shi, kuma kar ki fasa cire kaya gabansa tunda ke shashasha ce, sai kace warce bata taba shiga ajin islamiyya ba wai kina cire kaya gaban namiji da ba muharramin ki ba" Imaan ta nufi daki kamar xata yi kuka tace "Ni fa ba yanxu nake cewa ba Ammi, da da nake nufi, kuma naga ai yayana ne shi tunda ba ni da wani yayan" ganin Ammi ta yo kanta ta shige dakinta da gudu ta sa makulli tana turo baki kamar xata fashe da kuka. *Imaan* is not free subscribe and read hankali kwance🤷🏻‍♀️It's 300 via Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah Then u show ur evidence of payment via my WhatsApp digit 07087865788 to be included in the payment groupAmmi ce xaune parlon inna ta sanadin aikawa da innar tayi a kirata, ta fi minti sha biyar parlon amma inna bata ce da ita komai ba sai goge gogen kayan kallonta take, Ammi ta bukaci ta yi mata goge gogen inna tace ta bar shi, bayan wani minti biyar din Ammi tace "Inna na daura girki ne wllh...." Inna tace "Kin daura girki? Tabdi... Toh ita warcan 'yar da kika bari meye amfaninta da baxata dinga duba maki girkin ba, ina ce yau alhamis babu islamiyya" Ammi tace "Barci na baro ta tana yi" Inna ta tabe baki tace "A haka dai kullum, Allah dai ya mana tsari ya fidda d'a na kunya, amma gaskiya ni tunda nake tafasasshen ruwan Imaan bai taba shiga baki na ba, toh uwar me xata je ta dafa ma mijin ma idan tayi aure, kullum ayi ta laka ma yarinya ciwo ana daure mata kugu wai bata da lafiya, to ni dai ba ruwana ba wanda xai xagi d'a na, idan ma an samu to Allah ya isa" Ammi dai bata ce mata komai ba, Inna ta xauna tace "Tana yar yarinya da ita tayi ta langwabewa, tana abu salalo salalo, ana ma ciwo sharri to ni dai ba ruwana, dama magana nake son yi mama ke da Amina, to Aminar bata ga damar xuwa ba har yanxu, tana can sai ta mula ta mulmule sai kace xata ma Maryam haka....." Inna bata rufe baki ba Anty ta shigo da sallama, Tace "Sannu inna..." Inna ta tsuke fuska tace "Yauwa" Anty ta xauna tana kallon Ammi tace "Uwar Imaan kwana biyu" Ammi tayi murmushi tace "Ae kam duk mun buya" Mikewa inna tayi ta ci gaba da goge gogenta, Anty tace "Goge goge kike Inna" a fusace Inna tace "Toh baxan yi goge goge ba in mutu cikin wari yar nan, ko ke baki ga ko ina tsaf ba, ko hancin ki bai ji kamshin dake tashi parlon ba, wllh tun safe ban xauna ba ina ta aiki baki ji bayana ba kamar ya balle in huta, ke hatta simintin da kika tako kika shigo nan sai da na goge sa fess yau, ai kazanta bata da kyau, ni dai in sha Allahu cikin kamshi xan mutu ba ruwana, kuma tirr da kazami, ai ina lura duk cikin jikokina babu wanda ya dauko tsafta ta sai Mujaheed" Anty da Ammi dai sai kallonta suke, ta xauna tace "Yo Mujaheed mana, shi kadai ne Allah ya ceta ta wannan fannin, duk inda kazanta take ma shi bai xuwa, kullum tsaf xaka gansa abunsa, baxa ku yarda da xance na ba sai kun shiga dakinsa, ko don raino na ne shi din oho, ga shegen kyankyamin tsiya.... shi kuma wannan katon Isuhu ba shi da aiki sai saka gogaggun kaya da fesa turare amma duk kika basa abinci to wllh a nan xai bar maki kwanon ya tsallake ya wuce, to ina tsafta a nan, ai ta nan ake gane kazami, dakinsa kuwa karkari ya kakka6e gadon ya kara gaba, ita ko wannan mai laluran Imaan ga dai gashi har gashi amma ba gyara malam, kullum gashin nan a kume xa ki gansa sai ta fi sati da sattuka bata sharce ba, to ina tsafta a nan, da an mata magana sai tace xafi yake mata, ai duk mace ta gashi ake gane kazantar ta ni kwarkwata ma nake guje mata wllh, sannan babu tattali kullum sai ta bar min adikonta a nan idan ta xo, ga su can na tara yafi kala dari yanxu, Ko uwarta xan ci da su oho, ni ce ma Bukar xan yi ma ya daina siya mata turmin atamfa gwara a siya falle a mata riga da sket banda dankwali, Atoh shi kenan yayi ta asaran dukiya atamfa dai masu tsada amma tayi ta walakanta adiko, Maimoon kuwa dama kayan datti sai ta tara ta tara taga babu sarki sai Allah, babu wanda xata saka sannan xata kwashesu ta hau wanki duk su cika gida, to ina mace a nan, babu kazantar da ya fi wannan wllh, sauran yan matan kuwa ni wani lkcn ma sai in ji kamar wari suke wllh...." Murmushi Anty tayi, Inna tace "Wallahi ba batun dariya ba, to dai kowa tasa ta fishshesa a gidan nan ba ruwana da kowa ta kaina nake, yanxu dai abinda yasa na kira ku ba wani abu bane...." sai kuma ta yi shiru, su dai kallonta kawai suke, tayi kasa da murya tace "Ku lissafa min daga ranan asabar xuwa yau kwana nawa kenan" Ammi tace kwana shidda" Inna tace "Toh yau kwana shidda rabon Mujaheed da Imaan su xo min nan su gaisheni, yanxu fisabillahi daga sun min ba dai dai ba na nuna bacin raina sai su kullace ni, meye laifina don nace ban yarda shanye min fura da suka yi ba" Anty ta bude baki tace "Gaskiya basu kyauta ba har kwana shidda" Inna ta fara matsar kwalla tace "Ni fitinata har ya kai Mujaheed ya ki takowa nan yau har kwana shidda, daga gyara kayanka sai ya xamo sauke mu raba? Ke Amina na kira ki ne a matsayin uwarsa don ba ruwana da wancan katuwar da ta haifesa, ke kuma Aisha saboda Imaan yar ki ce" Anty tace "Amma Inna ca nake kince kada su sake xuwa maki idan ba haka ba xaki bar gidan" Inna xaro ido tace "Oh oh Allah kaji wata magana don Allah, to Amina idan na bar gidan nan ina da gidan uban da xanje in tsugunna, duk ba xance bane dai da tsorata mutane, bacin rai ai babu abinda bai sawa, don nace kada su sake xuwa kowa yasan fada kawai nayi, me suka min da xan hanasu xuwa nan?? Allah ya tsine ma fura da nonon in dai saboda shi xan kori jikokina, meye kuma wani fura da nono kamar mayyar bafillatana" Anty na danne dariyar ta tace "Ahh to gaskiya basu kyauta ba" Inna ta kalli Ammi tace "Ke kuma Aisha kinyi shiru kina kallona ko baki da abun cewa ne?" Ammi tace "Kiyi hakuri Inna, ina komawa xan sameta" Anty tace "Nima Mujaheed na dawowa aiki xan samesa In sha Allah" Inna ta gyara xama tace "Toh, sai ku ji dalilin da yasa xa su min haka su kaurace min, yanxu duk saukin kai na su basa gani, ni ba mafadaciya ba, ni ba fitinanna ba, ni ba mai sa ido ba, ni ba mai kwadayi ba, ni ba mai mita ba, toh meye xasu wani dauke kafa daga magana dai ta fahimta, to sai dai idan Ahmadu ne ya hure masu kunne ya masu hudubar tsiya, banda haka su har wani wayo garesu da xasu dauke kafa daga xuwa inda nake" Anty ta fara dariya, Ammi kam murmushi kawai tayi, Inna tace "Aa don Allah ku duba xancen da kyau, wllh xuge su aka yi, kuma ba kowa xai yi hakan ba sai mutumin nan Ahmadu don Bukar baya haka shi, ni gaskiya na ma daina sa Ahmadu a lamarina daga yanxu tunda tsanata yake cusa ma yaran a rai, anjima kuma xan sa kira min Bukar yaji abinda ake ciki, kwana daidai har shidda fa" Ammi ta mike tace "Ki yi hakuri Inna ina komawa xan mata magana bari in je in duba girki na" Inna tace "ke ta girki ma kike ga maganar al'ajabi ana yi a nan Ahmadu ya xuge yara, haba don Allah abinci dai abinci dai kamar ana yunwa Amina" Ammi ta nufi kofa tace "Toh sai dai anjima inna" Inna tace "Toh Allah bamu alkhairi, ki dai tsitsiyeta kiji dalili" fita Ammi tayi parlon bayan ta ma Anty sallama. Inna ta tabe baki tace "Kinga bafillatanin mutum, kinga agwai?? Wllh ki ji tsoronsa, barin idan kika ga ya fiye shiru shiru banda haka ki ga fa babu abun kirki da tace har ta bar parlon nan, Bukar dai na ganin boni, mata kamar kurma, ni kwanciyar hankali na ma Imaan bata dauko halinta ba, Imaan xata iya kwatar kanta a ko ina da bakinta, tun daga ranan da na karanta mata ta daina gaida Uwar Mujaheed gashi har yau bata gaisheta, gashi har Ahmadu da Bukar sun gaji sun kyaleta, kusan ma Imaan ce kadai ta dau halina a gidan nan wlh, banda haka ya xata dinga gaida katuwar mata bata amsa mata, da ta fi ta iskanci kuwa kinga ta daina gaishetan gaba daya" Anty dai dariya kawai take, Inna tace "Toh ni dai ki taimake ni Amina ki rufa min asiri, Mujaheed na dawowa ki titsiyesa a daki kiji me na masa da ya dauke kafa a nan" Anty tace "In sha Allah Inna, bari in je nasan ma ya dawo yanxu tunda biyar har ta yi" Inna tace "To yi maxa" tashi Anty tayi ta mata sallama ta fita inna ta mike ta ci gaba da goge gogenta tana cewa "Ahmadu dai ya lalace, da dai ba haka yake ba" Dariya sosai Imaan ta dinga yi bayan Ammi ta bata sakon inna, tayi mai isarta ta mike daga kwancen da take tace "Ba Inda xanje Ammi, tun Sunday kinji ta kai karana gun Abba, to haka ya fi, ita da bakinta tace wannan time din ba wasa take ba Abba ya ja mana kunne sosai don muna xuwa part dinta xata tsallake ta gudu ta bar gidan" Ammi tace "Toh nace bayan magrib kije ki gaisheta, kina gaidata ki juyo" Imaan ta fashe da kuka ba hawaye tace "Ammi don Allah ni baxan je ba, ina xuwa xata ce na mata wani abu" Ammi ta mike tace "Toh idan na baki abincin ki kai mata kar ki kai" daga haka Ammi ta bar parlon, Imaan ta fara kukan gaske, har ranta bata son xuwa gun inna. Anty na gama girkin dinner dab da magrib ta fito kitchen, ganin Mujaheed xai fita masallaci tace "Dr idan ka dawo mosque ka sameni bedroom" Yace "Toh" daga haka ya fita parlon, tare suka dawo masallacin da Yusuf, bayan sun haura sama Mujaheed ya shiga dakin Anty, Yusuf ya shiga dakinsa, Anty na xaune kan darduma ta shafe addu'o'in da take ta mike ta dauke pray mat din ta linke tana kallonsa tace "Toh ka tsaya min kamar soja a kai ka xauna" murmushi yayi yana shafa kansa ya xauna gefen gadon, tace "Yanxu M.A idan kowa ya guji inna kai ma sai ka gujeta" ya d'an buda ido yace "Inna kuma?" Tace "Eh mana" yace "Ban gane ba Anty" tace "Kirana tayi daxu wai kwana shidda rabon da kaje bangarenta kai da Imaan" Mujaheed yyi murmushi bai ce komai ba, Anty tace "Toh ka gama murmushin ka tashi ka ta fi ka gaisheta" mikewa yayi yace "Wa?? Ai har abada ni da xuwa apartment dinta, beside irin warning da Abba ya min ma is not funny don haka..." Anty ta karasa masa tace "Baxa kaje ba koh?" Yace "Allah Anty kinga kwana biyu shiru bata ce an mata komai ba hakan bai fi ba?" Anty tace "Toh ni dai nace ka tashi ka je" ya mike xaune yace "Anty ki bari kawai ba inda xanje" Anty tace "Wato ban isa da kai ba kenan, idan Hajiya ce tace kaje xaka ce mata ba xa ka ba?" Yayi murmushi yace "Anty Hajiyan ma hanani xuwa bangaren tayi gaba daya" Anty tace "Toh tashi ka fita ka ban waje" ya marairaice mata yace "Wllh Anty ina iya xuwa yanxu tace nayi mata wani abun" Anty ta hade rai tace "Cewa nayi ka gaisheta kawai ka juyo" Ya lumshe ido ya bude yace "Wllh da ba don ke bace ni ba inda xanje Anty" Anty tace "Naji din tashi ka fita, idan ka dawo kuma ka xo ka gaya min, gobe da safe kuma xan je in ji ko ka je" Murmushi yyi ya mike ya fita dakin. Tun da Imaan ta fito parlonsu rike da warmer din abinci take tsaye jikin wani flower taki tafiya, kiris ya rage ta fashe Inda take tsaye, daga nisa ta hango Mujaheed yana tahowa waya kare kunnensa, labewa tayi ta koma bayan flower din ta tsaya da sauri, sai da ya d'an wuce inda take ta fito tayi wani kara a bayansa, still yyi na few seconds, ta fashe da dariya ya juya yana kallonta, ya wani hade rai yace "Kee" Ta wara manyan idonta tace "Toh ai baka ji tsoron ba ma" Wani kallo ya dinga mata, ta turo baki ta wuce sa, sai da ya ga tayi nisa sannan ya bi bayan ta, tsaye ya ganta tana lekan parlon inna don kofar ba duka aka rufe ba, ya cire takalmansa outside the balcony yayi tiptoeing har bayan ta, fingers dinsa ya kai gefen cikinta yayi tingling dinta, ihu ta fasa ta sake abincin hannunta, tuni ya janyeta wajen don gaba daya tuwo da miyar dake warmer din ya tarwatse a kasa, ta xaro ido a rikice tace "Innalillahi yaya ka xubar" daga cikin parlor inna ta dinga cewa "Me aka 6arar??" Ummi ta bude kofar, Imaan dai sai kallon abincin take kamar xata yi kuka, Inna ta mike ta taho wajen tace "Meye hakan?" Kamar xata yi kuka tace "Yaya ne ya xubar da abincin da na kawo maki" Inna tace "Toh sai ki kwashe ki mayar mata ta canxa min wani ba ruwana" Imaan ta shige parlon ta xauna ta rungume hannu tace "Salon Ammi ta doke ni ba ga abinci nan Ummi ta kawo maki ba" Inna tace "Aa wllh kinga ina cin wani abu banda tuwo, Ummi maxa kwashe ki kai ma Aisha kice yar ta ta xubar ta xubo min wani" Ummi tace "Mu ma fa tuwo muka yi" A fusace Inna tace "To ni ina ruwana da tuwon ku? Ku tuwon ku har wani dadi garesa miya kamar an wanke kai, ki min abinda nace kada ran kowa ya baci a gidan nan" Ummi ta mike a fusace ta kwashe tuwon ta mayar cikin warmer din, Imaan tace "Dama kice yaya ne ya xubar na ni ba" Inna tace "Haba dai, dama ina xa ki iya xubar da wannan abincin ai sai dai shi" Tsallake miyar Mujaheed yyi ya shiga parlon ya xauna, Ummi ta tafi da abincin da ta kwashe part din su Imaan, gyaran wajen inna ta dinga yi duk suna xaune, bata gama ba Ummi ta dawo da wani abincin ta ajiye ma inna tace "Imaan Ammin ki tace xa ki dawo ki sameta" Inna tace "Sai me xai faruwa idan ta sameta, bakin cikin kara min abinci take komai, ina laifin ma tace xata gamu da Mujaheed din, Imaan ce ta wani san xubar da abincin mutane, bata ta6a ba tunda take, lafiya take kawo min abinci ta koma to yau da yake ta hadu da wnn mutumi a hanya" tana kai wa nan ta shiga parlon tana kallon Ummi tace "Don Allah ki rufa min asiri ki taimakeni ki karasa goge wajen baki ji bayana ba kamar xae cire" Ummi tace "Toh su da suka xubar...." Kallon da Mujaheed ke mata yasa tayi shiru ta mike rai ba dadi ta fita ta ci gaba da gyaran wajen. Inna ta shiga daki sai ga ta ta fito da bowl na dambun nama, tace "Tun ranan litinin nake ta ajiya amma ban gan ku ba na nace to ko lafiya, na ba kowa nasa...." Mujaheed ya amsa yace "Na waye wannan din?" Tace "Na kai da takwara ta" Ya saci kallon Imaan, da sauri Imaan tace "Inna ni dai ki raba mana da kanki" Mujaheed yace "Toh samo leda sai ki raba mana" komawa daki Inna ta yi, Mujaheed ya mike kafin Imaan ta ankara har ya fice parlon, kwalo ma inna kira ta yi, ya saka takalminsa ya kara gaba, inna ta leko parlon tace "Lafiya!" Imaan ta fara kuka tace "Ya tafi da naman gaba daya" inna tace "Maxa tashi ki bisa in ya kama ki je parlon Ahmadu ki tafi" Imaan ta mike ta fita parlon, bata son gudu saboda laluranta, hakan yasa kafin ta iske sa har ya shige part din su, ta goge hawayen da ya cika idonta a ranta tace "Allah ya isa" daga haka ta wuce apartment dinsu kawai, Sai da ta tsaya Ammi ta gama fadanta na xubar da abinci da tayi sannan ta shiga bedroom dinta. Bayan isha tana saka kayan baccinta wayar ta ya fara ring, duk tunaninta Sadeeq ne don kullum sai ya kira ta da daddare sun gaisa duk da basa waya mai tsawo iyaka gaisuwa shikenan amma har wani murna take idan ya kirata, Daddy ta ga ke kiranta, ta daga a hankali tace "Ina yini daddy" yace "Lafiya lau Mamana, ya gida?" Tace "Alhmdlh ya aiki?" Yace "Da godiya, kina karatu sosai dai koh?" Tace "Ehh ina yi" yace "Maa sha Allah, daxu kafin magrib inna ta kirani wai sati daya kenan baki je gaisheta ba, why is that?" Imaan tace "Daddy na fa je yau" Daddy yace "All those days me ya hanaki xuwa?" Tace "Cewa tayi kar mu sake xuwa ni da yaya fa" yace "That's because kuna mata rashin kunya ke da shi, wato warning da na maki kafin in tafi went in vain koh?" Shiru tayi bata ce komai ba, yace "Toh kar ki sake skipping one day baki je gaisheta ba, idan Ammin ki ce don ta maki fada xa ki k'i xuwa gaisheta, she is my mother Imaan you have to respect her much, shi ma Mujaheed na kirasa ban samesa ba ki kai masa waya yanxu" Kamar xata yi kuka tace "Toh" daga haka ya katse wayarsa, Hijab ta sa har kasa ta fita, Ammi dake parlor tana kallo ta bi ta da ido, Imaan tace "Daddy yace in kai ma yaya waya" Ammi tace "Shi me ya samu wayarsa?" Bude hannu tayi alamar bata sani ba, Ammi ta ci gaba da kallonta, hakan yasa ta nufi kofa ta fita. Babu kowa babban parlon nasu don hatta kayan kallo ma a kashe suke, ta haura sama ta na kallon direction din dakinsa don har ta manta rabon da ta je wajen, takawa tayi har bakin kofar sannan ta bude tana lekan cikin bedroom din, wani sanyayyen kamshi me hade da sanyi ya doki hancinta da fuskarta, shiga dakin tayi ta kulle kofar, ko ina fes har kan gadon dake dauke da farin bedsheet, Ko ba a fada mata ba tasan wanka yake jin saukan ruwa da kamshin sabulu da ya hadu da kamshin dakin, xaro ido tayi tana kallon sketches dinta dake bangon dakin kusan gudu hudu, tun tana Jss3 tayi drawing din mai kyau coz she is more than perfect a zane, turo baki tayi ta dau kujeran dake gaban mirror ta kai jikin bangon ta hau ta dinga cire hard carbon paper din a hankali kar ya yage. Bude kofar bathroom Mujaheed yyi ya fito da short yana goge gashin kansa da karamin towel, xaro ido yyi yana kallonta da mamaki, ta juya jin an bude kofa suna hada ido ta turo baki tace "Yaya daddyna yace in kawo maka waya" Tana magana wayarta da ta ajiye kan gado ya fara ring, sakkowa tayi da sauri ta dau wayar tace "Ga shi nan ya kara kira" daga haka ta nufesa ta daga kiran ta kai kunne tace "Daddy ga shi nan" mika masa wayar tayi ya amsa ya kai kunne hade da sallama, Kamar ance ta juya taga bowl din dambun naman da ya dauke ajiye a gaban mirror dinsa, yana magana da daddy amma duk hankalinsa na kanta kuma yana lura da ita, ganin ta nufi gun mirror din ya fixgota, xaro ido tayi xata yi magana ya rufe bakin, sai ce ma daddy yake toh don ya kagu ya katse wayar, kamar kuwa daddy ya shiga ransa yace "Shikenan we will talk tomorrow sae da safe" da sauri yace "Allah ya tashe mu lafiya Abba, mun gode, sae da safe" daga haka ya katse wayar ya juyota yana mata wani irin kallo yace "Drawings din da kika cire nake so ki hau kujeran ki maida su yanxu kafin ki fada min sanda na fara wasa da ke da xaki shigo min daki kai tsaye" ta 6ata fuska tace "Toh ba waya na kawo maka ba" Jan kunnenta yayi yace "Baxa kiyi knocking idan kinji ba a amsa ba kiyi wucewar ki" muryar Umma suka ji a corridor tana ma Maimoon masifa wai ta share datti ta kai bakin kofarta lkci daya kuma tana tambayarta ko Mujaheed na dakinsa, Maimoon da ta hade rai tace "Yana ciki" Mujaheed ya xaro ido ya ja Imaan ya bude kofar bathroom dinsa suka shiga ya kulle kofar, dai dai nan kuma Umma ta shigo dakin tana kiran sunansa, Irin tsoratan da imaan tayi ba a cewa komai, Mujaheed ya dukar da ita kasan bayin murya can kasa yace "Kee you better relax now kar in mare ki, ance maki xata shigo nan ne" kai kawai take gyada masa numfashinta na sama, ya cire Hijab din jikinta yace "Nace maki ba fa shigowa xata yi ba, breath in and out gently now" jingina take son yi da bango ya jawota jikinsa ya rungumeta yana shafa bayan ta a hankali to calm her down, tuni Umma ta fice dakin ganin Mujaheed bai ciki, bayan kusan minti biyar jin tana fitar da numfashin a hankali kuma a nutse ya dago kanta yana kallonta, hawaye ne makale idonta, ya daure fuska yace "What?" A hankali ta nuna masa kirjinta, ya mike ya fita bathroom din ya sa makulli kofar dakin sannan ya dawo ya fito da ita dakin, wajen da yake ajiye drugs da allura ya bude yana dube dube, can kasa ya hango inhaler dinta da take bari a dakinsa a da idan ta xo, ya juya ya kalleta ya ga kwanciya tayi kan gadonsa ta takure waje daya, ya mayar da inhaler din ya mike, ya dau gogaggen jallabiyarsa ya saka don tuni jikinsa ya bushe, ya feshe jikin sa da turare, ya dau drawings da ta ciro ya fara maidawa jikin Bangon, Imaan ta mike xaune tana turo baki xata ce masa don me idonta ya kara sauka kan dambun dake gaban mirror, tashi tayi a hankali har sannan hannunta na kirjinta ta isa gaban mirror din ta dau bowl din, karan bude kofar da yaji ya sa ya juya, xata fita da gudu ya bi bayanta da sauri yana cewa "ke har kin manta abinda ya same ki a bathroom ynxu koh, ba ruwana fa idan...." Tuni ta fara sauka stairs, sai da ya tabbatar ba kowa corridor sannan ya bi bayan ta da sauri, amma har ta fita gidan, can ya hangota a durkushe kusa da apartment dinsu, karasawa yyi kusa da ita a hanxarce, ya durkusa kusa da ita yace "Ba nace kar kiyi gudu ba..." Dagata yyi ganin Asthman ne ya tashi ya amshi bowl din, ya wuce da ita cikin apartment dinsu, Ammi ta tabe baki ta mike ta dauko inhaler ta jefa masu, sai da ya ga numfashinta ya dawo dai dai sannan ya mike ya dau bowl din naman ya ajiye a kafarta yana mata wani kallo ya fita parlon, a hankali take sauke numfashi ta bude bowl din ta fara cin naman. *The book Imaan is not free, it's for sale, you read for free ur cup of coffee*🤷🏻‍♀️ It's 300 via Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah Then u show ur evidence of payment via my WhatsApp digit 07087865788 to be included in the payment group.Ranan Friday Imaan suka gama exams din first term ss2, suna tsaye tare da Mariya a bakin gate din makarantar tasu ko wannensu na jiran driver, Ummi da Rahma ko fitowa cikin schl din ma basu yi ba, Maimoon dai na tare da wata Kawarta a waje ita ma, Mariya na ganin motar Sadeeq tace "Lahh ya Sadeeq ne ma ashe shi sa ya bata mana lokaci" Imaan dai bata ce komai ba, tunda yayi parking idonsa ke kan Imaan, suna had a ido gabanta ya fadi, siblings din sa duk suka shiga motar, Mariya bata taba sanin Yayan nata na interacting da Imaan ba don Imaan din bata gaya mata ba, Mariya tace "Mu je ku gaisa da shi, shine ya ta6a ajiye ki gida ko baki gane sa ba" Imaan ta d'an yi murmushi kawai, Mariya ta kama hannunta suka nufi gun motar, Mariya tace "Ya Sadeeq frnd dita da ka taba ajiyewa a gida..." Ya cire glass din idonsa Yace "Yea na gane ta" Imaan ta sauke idonta kasa tace "Ina yini?" yace lafiya lau, fatan an gama exams lafiya" tace "Alhmdllh" yace "Toh Allah bada result mai kyau" ta daga kai tana kallonsa tace "Ameen" lallausan murmushi ya sakar mata ta dauke kai da sauri gabanta na faduwa, yace "Let drop u mana" ta girgixa kai tace "Aa yanxu driver din mu xai xo" Yace "Ohk then" ta saci kallonsa ya kashe mata ido daya, ta daga ma Mariya hannu ta juya da sauri ta tafi gun Maimoon, Sadeeq ya tada motar ya bar wajen, Ya Yusuf ne ya xo daukansu bayan tafiyar su Sadeeq da kusan minti bakwai, Maimoon na turo baki tace "Ya Yusuf driver din fa?" Yusuf yace "Ya kai su Umma kasuwa, M.A aka ce ya dauko ku tun daxu ya ki, ni kuma ynxu na dawo aiki" Maimoon ta kyabe baki tace "Da dai Anty Farida aka ce yaje ya dauko, jiya fa da yamma har Hayin d'an bushiya muka je daukota taje gidan aunt dinta, baka ga uwar wahalan da muka sha ba ga hold up sai kusan shidda da rabi muka dawo gida" Yusuf yace "Au suna tare har yanxu kenan?" Maimoon tace "Tab, sosai ma, gobe xata koma schl sai kaga tulin shopping da yayi mata" Yusuf ya sake baki yana kallonta, Maimoon ta kyalkyale da dariya tace "Amma fa wllh ya Yusuf kar ka ce masa komai, dama yace kar in fadawa kowa" Yusuf yace "Ae ko kin fada ma kowa tunda kika fada gaban Imaan da Ummi" Imaan ta hade rai tana kallonsa ta madubi tace "Ya Yousuf kamar ya?" Ya wara ido yace "Ke sai ki kwasa ki kai ma inna, Ummi kuma ta gaya ma Umma, saukin abun dai idan magana ya fita an san it's either Imaan or Ummi sae M.A ya ji dadin jibgarku da kyau" Imaan ta xumburo baki tace "Naji dai" Ummi kuwa yi tayi kamar bata ji sa ba dama, suna isa gida Maimoon tace "Dama ya Yusuf ka ja masu kunne ba ruwana idan suka fada ma kowa" wani kallo Imaan ta watsa mata ta fice daga cikin motar tana turo baki ta kara gaba. Satin da aka shiga banda shirye shiryen bikin Seeyamah babu abinda ake a gidan, tun ranan lahadi yan uwa suka fara xuwa daga nesa gida ya fara cika da jama'a, kowa ya xama busy a gidan barin Umma da Anty, Ammi kam baya baya ta dinga yi, tun a ranan lahadin dama ta kai nata gudunmawarta na tsadaddun manyan bedsheets biyu, da set din food warmer shi ma biyu masu kyau sosai, a walakance Umma ta dubi kayan aka bar su a nan parlorn. Ranan laraba Abba ya ba su Maimoon kudin gyaran gashi da lalli a kai su Saloon, Har xa su fita ya dakatar da su ya ciro wani dubu biyar din yace "Na mance ban bada na mamana ba, gashi nan ta shirya ita ma ta je" Fita suka yi su hudu Ummi na cewa su yi wucewansu kawai don Imaan ba xuwa xata yi ba, Maimoon tace "Ba ruwana Abba cewa yyi mu je mu kira ta" A balcony suka tadda Anty tana magana da wa enda xa su yi girkin biki a biya su, Mujaheed ma na xaune balcony din sai Yusuf dake tsaye, Anty tace "Saloon din xa ku yanxu" Maimoon tace "Anty Abba yace mu je da imaan" Anty tayi wani dariya tace "Wace Imaan din tab, amma ku je dai ku ji abinda xata ce" Imaan na dakinta Maimoon ta shigo parlor, nan ta sanar ma Ammi abinda Abba yace Ammi ta kira Imaan, tana fitowa Ammi tace "sai ki dau Hijab ku wuce saloon" sosai gabanta ya fadi ta marairaice tace "Saloon kuma Ammi, aa ni dai xan wanke gashina da kai na" Ammi tace "Kee! dau Hijab ki fice min parlona, dama idan baki gyara gashin nan ba yau kar ki dawo min gidan nan" Imaan fa fashe da matsanancin kuka tana kallon uwar tata, ganin Ammi ta mike ta shiga daki da sauri ta dau Hijab dinta ta fita, Maimoon ta bi bayan ta tana dariya kasa kasa, Anty na ganinta tace "Subhanallahi me ya faru Imaan" cikin kuka tace "Anty ni fa gashina bashi da wani datti kawai combing dinsa ne bana yi" Anty tace "Toh mu ga gashin" tana shesshekar kuka ta cire Hijab din ta cire hulan kanta, Yusuf ya dauke kai bai son dariya ta fara wani sabon kukan, ga dai gashi har gashi amma duk an cukuikuye shi waje daya, Anty tace "When last kika wanke gashin" a hankali tace "Ranan nan" Anty tayi murmushi kafin ta ce komai Mujaheed ya mike fuska daure yace "Mu je in kai ku saloon din" Ta fashe da sabon kuka xata koma bayan Anty ya ja ta sai gun motarsa, Yusuf yayi murmushi yace "Da yake Umma bata nan ba" Su Maimoon duk suka shiga motar bayan ya tura Imaan ciki, Suna isa saloon din Imaan ta hadiye kukan da take barin da taga yan mata kala kala cikin saloon din, Ita Mujaheed yasa a fara gyara ma gashin, da ruwa mai dumi sosai yace a wanke mata gashin nata bayan an sa mai, banda turo baki bbu abinda take tana runtse ido don ba daman kuka ga yan mata kar su mata dariya, lkci daya gashinta ya dawo sak na Indians sai sheki yake, ganin an kusa gama mata ya kalli kannin nasa yace "Sai ku samu napep da xai maida ku gida, coz I am a driver to none of you" daga haka ya fice saloon din, duk suka bi sa da kallo. Sai bayan magrib suka shigo gidan don har da lalle suka yi, dama Imaan direct part din inna ta nufa tun daga bakin kofa ta cire Hijab din jikinta ta shiga tana murmushi tace "Inna..." Inna tayi mitsi mitsi da ido tana kallon gashin nata tace "Ikon Allah kin ganki kin fito sak mace ko?" Imaan ta xaro ido tace "Toh da ni na miji ne?" Inna tace "Idan ba kallon isuhu nake maki wani lkcn ba shegiya nake" Imaan ta fashe da dariya har da kwanciya kan kujera, Inna ta kalli Mujaheed dake cin abinci tace "Ko kai baka gani ba Mujaheed?" Imaan ta hararesa ta gefen ido ta mike xata shiga daki Inna tace "Dawo nan ana ma yar uwar ki gyaran jiki tunda can bangarensu ya dawo kamar wajen cin kasuwar laraba" Imaan tace "Anty Seeyama" Inna tace "Ehh kema da dai Allah ya fiddo maki da mijin nan kiyi aurenki da wuri ki haifi kanninki da uwarki taki haifo maki" Imaan ta hade rai tace "Yar karama da ni xaki ce min aure?" Inna ta kalli Mujaheed tace "Don Allah Mujaheed Imaan bata isa aure ba yarinyar da ke al'ada? Ga kirjinta cike da dukiyar fulani" Murmushi Mujaheed yyi kansa a kasa yana cin abincinsa, Imaan ta harari Inna ta juya ta nufi kofa inna tace "Ke kika sani, ni ba ruwana wllh, Allah na tuba lalurorin ki na duniya ma ai tsaye yake da kafafuwansa gun d'a na, ba gwara kiyi auren ko Bukar xai huta da kashe kashen kudi kije can kuma mijin shi ma ya d'an dana ukubar" Washegari alhamis Imaan ta tashi da ciwon ciki ga bak'i a part dinsu balle tayi raki yanda ranta ke so, duk magungunan da ta sha ba wanda taji ya mata, ta lallaba da kyar ta tafi bangaren inna, ita din ma dai parlon nata duk tsofaffin kawayenta ne a xaune, imaan ta gaishesu da kyar ta shige bedroom dinta ta kwanta, lkcn Azahar nayi dama inna ta lallabo ta shigo dakin ta sa ma bandakinta makulli don ba wanda xai shiga balle ya mata kazanta duk me son yin alwala ga pampo can ta bude, idan kuwa xai kama ruwa ne to yaje sashin masu biki, ganin juye juyen da Imaan take duk ta hada xufa duk da iskan fankan dake dakin ta wani xaro ido tace "Ke lafiya meye hakan, ni fa ba ruwana idan baki da lafiya ne ki tafi bangarenku kada a gigitani a nan, meye wani juye juye kamar macijiya a kan gado na" Imaan ta fashe mata da kuka tace "Wayyo cikina ke min ciwo" Inna tace "Auzubillahi, to rufa min asiri ki sakko ki tafi gun uwarki ba ruwana" Cikin kuka tace "Akwai mutane a can" a fusace Inna tace "Mutanen banxa ina ruwanki da su, idan wani abu ya sameki maganin me mutanen xa su yi banda su cika mu da surutu, dama ba komai ya kawo su ba sai kwadayin d'an shinkafar da xa a raba a kwano da kaji banda haka wani ma anyi shekara goma ba a gansa ba, ki tashi ki tafi tasan yanda xata yi dake idan ma asibiti ne ta kai ki, idan ko ba haka ba idan ban sa an dage bikin ba ace bani ba, biki ya fi rai ne" da kyar Imaan tace "Ni fa marana ke min ciwo" Inna tace "Wai jini?" Imaan ta gyada mata kai, Inna tace "Toh shi kuma wanda kika yi ko sati ba ayi ba fa?" Tace "Ba shi bane kawai alama ne" Inna ta xabga tagumi tace "Ke kam kina ganin jarabawa iri iri a rayuwa na lalura, banda haka jinin ma idan xakiyi sai kin ta fama, anya kuwa ba a sa maki hannu ba imaan?" Imaan ta xamo daga kan gadon tace "Wayyo ni dai ki kira min yaya " Inna tace "Waye kuma yaya?" Hawaye na sakko mata tace "Ni dai ki kirasa" Inna tace "Toh su wa encan tsofaffin duk tsami sun cika min parlor kamar ni xan aurar da 'ya sun ki tafiya, ni dai na gaji wllh ana damuna, wata ma ni nafi shekara talatin ban gan ta ba, ni dai gaskiya sun isheni suje can bangaren da ake biki kuma sun ki, duk parlona ya gauraye da warin tsofaffi, wannan fitina da mai yayi kama" Imaan na son yi dariya amma ciwo yaki barin ta tayi, Inna ta fita fuska daure ta kashe TV da ke aiki tace "Kada TV ya buga in ja ma Ahmadu asara gwara a bar shi haka nan ya huta" daga haka ta dau wayarta ta fita don neman me kira mata Mujaheed, wata ta samu a tsakar gida ta nufeta tana kallon mata yan gayu xaune tsakar gidan, tace "Toh dai gida ba na bitilman bane duk wanda ya xubda ko kwayar shinkafa yyi hakuri ya share fisabillahi, kar a tafi a bar mu cikin wari cuta ta kama mu" mika ma matar wayar tayi tace "Gashi Idan kin iya karatu ki duba lambobi xa ki ga ansa Dakta, lambar Mujaheed ne shi ya sa mun shi a haka, sai ki kira min idan kuma baki iya ba don Allah kar ki rikita min wayar in shiga uku" murmushi matar tayi ta nemo number tayi dialing ta mika ma inna, ta amsa ta kai kunne, sai da yayi ringing sau uku sannan Mujaheed ya daga, inna tace "Mujaheed??" Mujaheed yace "Ina ji, ya aka yi?" Inna tace "Toh ga yar uwar ka nan dai rai a hannun Allah, duk inda kake ka rufa mana asiri ka juyo ka dawo, ni sae in iya cewa a daga bikin ma wllh don idan ta mutu ni nayi asara...." Da mamaki yace "Wacece?" Inna tace "Wacece banda Imaan, tun safe Ashe tana dakina babu inda bata mirgina ba don ciwo, tun daga kan gadon har kasan tass, wai yanxu na shiga dakin don kulle bandakina saboda marasu hankali masu shiga bayin mutum suyi kaca kaca da shi kawai naga yarinya duk ta hada xufa a kan gado kai kana ganin ta kasan...." Mujaheed ya katse ta yace "Ina hanya" daga haka ya katse wayar, Inna tace "Atoh haka kawai, bikin banxa bikin hofi..." Daga haka ta nufi part dinta, tana durkushe bakin kofa tana watsi da takalman jama'a can gefe ganin duk ya cika mata bakin kofar ta ji muryar Mujaheed a bayan ta ta mike, tace "Wannan uban sauri haka kamar wanda ya biyo jirgi, to ka shiga tana can ciki ban san isilinta ba" Shiga parlon yayi ganin mutane ya sunkuyar da kansa ya gaishe su ya wuce dakin Inna, karasawa kan gadon yayi yana kallonta yace "Me ya faru?" Ta fashe da kuka sosai tace "Yaya cikina" hannu ya kai cikin yace "Tun yaushe?" Ta cire hannunsa tace "Ni ba cikin bane ke min ciwo, period ne" ya daure fuska yace "Toh me xan maki, ba kin sha magani ba" da kyar tace "Bai yi ba, doctor Habib allura yake min" yace "Toh me ya hanaki kiransa?" Tace "Yana Lagos" yace "Toh bani da allura a nan sai na koma asibiti" ta kamo hannunsa cikin rawar murya tace "Toh ka tafi da ni asibitin plss" tana fadin haka ta fara kokarin sauka kan gadon, bude baki yyi ganin yanda tayi ma inna stain din kan gado, bai san lkcn da ya dauke kai yana murmushi ba don har ya hango inna, ita ma xaro ido tayi tace "Na shiga uku yaya" yace "Aa sai ta gani xaki ki shiga ukun ai, yanxu kina daya ne" ji tayi gaba daya ba ciwon ta sauko kasa da sauri jikinta na rawa tace "Wayyo yaya ya xan yi" Tana fadin haka ta nufi bathroom ta murda ta ji a rufe, tsayawa kallonsa tayi kamar xata yi kuka tace "Yaya ta sa makulli" parlor ya koma gun inna yace "Inna xata shiga bayi ina makullin" inna ta mike da sauri tace "Auzubillahi, wani bayin? Aa ta fito ta tafi nasu idan ma baxata iya tafiya ba ka goyata, haka kawai bayina fess ta shiga ta sa min k'arnin jini" Kunya ma yasa Mujaheed ya kasa cewa komai don mutanen dake parlon sun kai shidda, ganin inna xata shiga dakin ya rigata shiga da sauri, ya dau dankwalinta ya rufe saman gadon da shi, Imaan ta marairaice tana kallon inna da ta shigo tace "Don Allah ki ban makulli wllh xan wanke maki bayin" Inna tace "Ai uwata bata ce min je ki kya gani ba, don haka ba bayina xa a shiga a min kazanta da jini ba, ki daure ki tafi can bangaren ku idan ma tafiyar ne baxa ki iya ba sai Mujaheed ya goya ki" Kuka Imaan ta fara yi tace "Na fa ce xan wanke maki wllh" a fusace Inna tace "Kai ku fita ma ku bar min dakina kuje can bangaren ku karata, da na bar ki ma kika kwanta min saman gado duk da ban san al'ada kike ba" Mujaheed yace "Toh ki bata xan wanke maki bayin da kai na" Inna kamar xata rushe masu da kuka tace "Yau naga abinda ya isheni bai ishi Allah ba, wai ana dole ne, hypo uku na xuba bayin nan daxu da safe da nake wankewa, a kan wani dalilin xa aje a bata min da karni...." Ya katse ta yace "Ni kuma xan xuba maki hypo biyar" da kyar da kyar da sidin goshi inna ta bada makullin shi ma sai da aka yi yarjejeniyar baxa a bude mata drum din ruwa ba kada a xuba kazanta, Mujaheed ya dau buckets biyu ya fita debo ruwa a waje, Ita dai imaan na tsaye sai satan kallon saman gado take, Mujaheed na ajiye ruwan a bayin ta bi sa ciki tace "Wayyo yaya pant da pad da xan canxa fa?" Ya kalleta da mamaki yace "Ni ma kike tambaya?" Ta marairaice tace "Plss ko xaka je dakina...." Ya jefa mata wani kallo yace "You are stupid" fitowa bayin tayi ta bude gun kayanta a wardrobe din inna, ai ko taga panties dinta na nan, tace "Yaya toh saura pad" Yace "Bari in xama pad din ki sa" Bata ce komai ba ta turo baki ta shiga bandakin ta rufe, juyawa yayi ya fita, ya tafi gun mai kiosk dake layin ya amso always daya ya dawo, inna dai na xaune ta daura kafa daya kan daya tace "Allah ni dai ya dubeni ya rabani da k'arni, komin xuba hypo da xa ayi a bandakin nan" Mujaheed bai ko kalleta ba ya shiga dakin, yana ta tsaye har Imaan ta fito daure da towel din inna, ya jefa mata pad din kan gado, ta turo baki tace "Thank you" komawa bandakin tayi ba a dau lkci ba ta fito, yace "Sai ki cire xanin gadon ki wanke" ta xaro ido tace "Yaya ya min nauyi fa" bude baki yyi yace "Toh ki bar shi haka nan" kamar xata yi kuka ta isa kan gadon ta shiga cire xanin gadon bayan ya dauke pillows din kai, Muryar inna suka ji tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, jinin ta xuba min a kan gado ni Asabe????" Inna ta fashe da kuka tace "Me na maki xaki saka min da haka Imaan" Mujaheed ya dauke kai yana kokarin danne dariyarsa, imaan duk ta gigice, inna tace "Toh sai ki Kwashi xanin gadon don ubanki ki Bukar kai ma Aisha ta wanke min, kai kuma ka fitar min da katifar waje ka sa min shi a setin rana, Allah ubangiji ya saka min, daga taimako sai ta xuba min al'adarta a xanin gado k'arni ya kashe ni" Inna ta kara rushewa da matsanancin kuka tace "Sannan d'an walakanci tana yoyon xata dau tawul dina ta daura salon ta goga min gaibu, ni dai na shiga uku da wannan 'ya ta Bukar, tana cutata a gidan nan" Imaan ta wani hade rai kamar xata yi kuka, Mujaheed ya cire xanin gadon ya wuce bathroom da shi, Inna na matsar kwalla ta daga hannu biyu sama tace "Allah kaga xuciya daya nake xaune da kowa gidan nan, duk mai nufina da sharri ka min iyaka da shi" Tana fadin haka ta share idonta ta fita tace "Bari xanje inji ko Aishar ce ta sa ki xo ki cuce ni yau" Imaan ta murguda baki ta fiddo kayanta a press ta saka, bude kofar bathroom din tayi ta ga Mujaheed yana aikin wanke xanin gadon.Imaan dai na tsaye har ya gama wankin bedsheet din tana rike da kayan da ta cire, ya saka xanin gadon a bucket ya fito, a hankali tace "Yaya to wankin bayin fa?" Wani mugun kallo ya watsa mata ya dau wayarsa da makullin mota da ya ajiye kan gado zai fita ta xaro ido tace "Yaya don Allah ka tsaya, baxan iya shanya bedsheet din ni kadai ba ai" ko juyowa bai yi ba balle ya tanka ta, a bakin kofar parlor ya hadu da Inna, Inna ta gwalo ido tace "Har an wanke min bayin?" Yace "A'a xan fita in amso Hypo ne" yana magana ne yana kokarin fita, inna ta cakumosa tace "Sai dai ka raina ma Bukar ko Ahmadu hankali, ce maka nayi bani da hypon?" tana fadin haka ta ja sa xuwa bedroom din fuskarta daure, yace "Toh ki sakeni mana" ko saurarensa bata yi ba har suka shiga dakin, Imaan dake labe bayan kofar dakin tana jin sun shigo dama ta fito da sauri ta fice a dakin, Har bandakin Inna ta turasa ta dauko Hypo biyu ta jefa masa, yace "Biyar fa kika ce Inna" a fusace tace "Toh ai ni ba asararriya bace Mujaheed, Ko sisin Bukar da Ahmadu babu a Hypon, Isuhu ne na roka ya siyo min" tana fadin haka ta dau ledan omo babba ta jefa masa tace "Har jikin tiles ni dai a gurje min ba ruwana, kuma daga yau gaskiya idan Imaan ta sake shigo min daki xa a ga bala'i, wato kawai fasa bomb din bala'i xanyi a gidan nan, naje yanxu uwar bata nan, da sai in ji ko ita ta turo min ita ta cuce ni ta xuba min al'adarta, banda ma kazanta irin na yaran ynxu duk sai sun bari kowa ya san suna al'ada, gantalalliyar duk ta tashi ta kazance min kan gado da bandaki, to hirrr dinta kada ko da wasa ta sake leko min daki ta tsaya iya falo, idan kuwa dama bata da tsarki kar ta yo min nan xan koreta don parlona na tsarkakakku ne" Mujaheed dai bai tanka ta ba ya nade sleeve din shirt dinsa ya fara wanke bayin bayan ya kada kumfa da hypo, inna tace "A'a bana son aikin al'gus malam, ka kara barbade bandakin da omo lungu da sako sai ka juye dayan hypon" ya jefa mata wani kallo yace "Toh wai ni na bata maki bandakin daga taimako kawai" Inna tace "A'a ba ruwana saboda kai na bude, in don ta wancan matar ce ai sai dai ta tafi bangarensu jage jage da jini don wllh baxan bude ba, haka kawai" ko kallonta bai yi ba ya ci gaba da wankin bayin da babu abinda ya samesa, haka inna ta dinga basa wahala tana tsaye daga bakin kofa tace can tace nan, har daga karshe aka gama wanke bayin, ya wanke hannunsa ya fito fuska daure, tace "Toh don Allah ni dai kar in kwana cikin k'arni yau ka taimakeni ka fidda min katifar can ka ajiye dai dai idon rana" yace "Wannan kuma sai dai ki kira Yusuf baxan iya ba gaskiya" Tace "Toh wllh baxa ka fita dakin nan ba sai tare da katifar nan, haka kawai in kwana cikin najasa, kafar ka kafar katifan" tana fadin haka ta sa makulli a dakin ta tsaya bakin kofa, kallonta ya dinga yi fuska daure, inna tace "Oho dai duk kanwarka ta ja maka, ita yanxu ba gashi ta gudu ta bar ka da aikin jini ba, yarinya sai mugunta fal cikinta" Babu yanda ya iya haka ya cire katifar ta bude masa kofa tace "Saitin rana xaka ajiye duk ya kona abinda ya xuba kai" fita yyi da katifar ya ajiye inda tace, ya dawo dakin don daukan wayarsa da makulli, ganin babu su a inda ya ajiye ya kalli inna dake tsaye tana kallonsa kyarr, bucket din xanin gadon ta nuna masa tace "Idan ka shanya wnn sai ka dawo ka amshi wayar ka da makulli ba ruwana, yarinya dai ta cuce ka kawai, sae dai sakayyar Allah" tana fadin haka ta koma parlor, Mujaheed ya fi minti uku a tsaye, yasan ko me xai ce mata baxata basa ba, hakan ya sa ya ja tsaki ya dau bucket din fuska daure ya fice dakin, yana gama shanyawa a nan parlorn ya ajiye mata Bucket din yace "Bani wayana in wuce" ta jefa masa makullin siff dinta tace "Ka bude ka dauka ka rufe min kayana" daukan makullin yyi ya koma daki ya bude yana daukan wayarsa da car key ya bar mata siff din a wangale ya fice kamar xai tashi sama, inna tace "Oho dai....." Dab da Magrib Ammi ta shiga tada Imaan dake ta bacci tun bayan da ta kara shan magani, Ammi tace "Ya jikin?" A hankali tace "Da sauki, Ammi Daddy ya dawo?" Ammi tace "Ehh ya dawo" wara ido tayi ta sakko kan gado ta sa Hijab har ta isa kofa ta tsaya ta juyo tace "Ammi hope bak'in duk sun tafi?" Ammi tace "Ina kuwa xa su gobe biki?" Imaan tace "Toh daddy yana bedroom dinsa ne?" Ammi tace "Aa ina jin suna can tare da Abba" Imaan na sa takalminta bakin kofa aka bude kofar parlon, d'aga kai tayi taga Inna ce, Inna tace "Ya jikin, na ji shiru tun daxu baki leko ba shine nace bari in lallabo in xo in duba ki, kun je asibitin ne?" Imaan da ta hade rai ta ki kallonta tace "Ni na ji sauki" inna ta amsa gaisuwar masu gaisheta a parlon sannan ta kalli Imaan tace "Tohhh, Allah dai ya sauwake, amma wannan wahala ba gwara Bukar ya aurar da ke ba kowa ma ya huta kema ki huta" Ammi dake tsaye tana jin su ita ma ta gaida inna, inna tace "Lafiya lau Aisha, in ji mai gidan ya dawo lafiya?" Ammi tace "Alhmdllh" Inna tace "Toh da kyau, duk da dai ni ko tsinke ba a kawo min a tsarabar da yake yowa, sai dai ke da yar ki ku cinye, to duk ba wannan ba don bai dameni ba wanda Ahmadu ma ke bani Allah ya amfana, yanxu dai xuwa nayi in duba jikin Imaan, ta xo daxu tana ciwon mara ban kai ga jik'a mata ararra6i ba na nemeta na rasa" Ammi tace "Ta ji sauki yanxu, sai dai ko ta bi ki ta amsa ta sha a can" inna ta gwalo ido da sauri tace "Ta bi ni ina? A'a ta xauna xan lallaba in koma in jiko mata in kawo yanxu, ta bi ni kuma ana xaune kalau? Taje ta min me kuma ban da abun ki Aisha yarinya na fama da kanta, Aa bari inje in dawo yanxu, dama na bar sauran tsoffin da basu tafi ba kada a min barna" daga haka ta juya ta bar bakin kofa murya can kasa tace "Haka kawai ta sake koma min ta min wani aika aikan da kazantar ta a gida ta cuce ni, wa gareni da xai bi min hakkina ban da Allah" Imaan ta turo baki ta fita parlorn ko da wasa bata fadi ma Ammi abinda ya faru daxu ba, part din su Maimoon ta nufa, kasa shiga parlon tayi ganin mutane a ciki, ta fi minti biyar tsaye bakin kofar taji muryar Yusuf yace "Me kike yi nan Imaan" kallonsa tayi tace "Toh akwai mutane a parlon ta ya xan shiga" tana magana tana kallon Mujaheed da ya wani hade rai don tare da Yusuf suke, dauke kai tayi bata son tayi dariya, can ta turo baki ta bar bakin kofar ya shiga ciki, Yusuf yace "Toh ko in maki jagora?" Dariya tayi tace "Daddy na yana parlon Abba?" Yusuf yace "Eh mana" tace "Toh oya ka shiga gaba sai in bi ka a baya" a haka suka shiga parlon tana boyewa a bayansa wanda hakan yasa few kawayen Umma dake parlon suka dinga kallonta har suka shiga parlon Abba. Da gudu ta tafi ta rungume daddy tace "Daddy sannu da dawowa" Daddy yace "Baki gaida Abba ba" kallon Abba dake kallonta tayi, ta boye fuskarta tace "Ina yini abba" yyi murmushi yace "Lafiya lau daughter" Daddy yace "Toh baki gaida yayanki ba shi ma" ta kalli Mujaheed dake parlon tace "Ai mun hadu a waje" Daddy yace "Toh maa sha Allah" Tace "Daddy baxan je gombe Hutu ba tunda mun yi holiday?" Abba yace "Wajen wa a gombe" murmushi Daddy yayi yace "Kanwar mamarta" Abba yace "Ohk If I recalled well last holiday ma can kika je ko" Kai ta gyada masa, Abba yace "Kuma babu canji, ga gwaggon ku Suleja ma ba sai ki je can ba ko da su Maimoon, dama bata da lafiya" Daddy yace "Gaskiya ne ya kamata" Imaan ta xaro ido tace "Kauye?" Abba yace "Of course, you will have more experience.... Shi kauyen ba wuri bane" Ta dauke kai bata ce komai ba ta cinno baki gaba, Abba yace "Nasan inna xata ji dadi idan taji xa ku je, kinga sae Mujaheed ya kai ku a mota tunda ya sha xuwa tare da mu" Da sauri Mujaheed ya kallesa yace "Abba... ai ba lalle xan gane wajen ba fa" Abba ya kallesa yace "Last time ma ba kai ka kai mu a mota ba" da kyar yace "Abba kusan shekara daya fa" mikewa Imaan tayi ba tare da ta kallesu ba tace "Xan je ina taya Ammi aiki" bata jira cewarsa ba ta fice, Abba yayi dariya yace "On a serious note dole su je riga suyi hutu bari dai a gama bikin nan lafiya" mikewa Mujaheed yyi yace "Xan je ana kirana can waje" daga haka ya fice a parlon, Daddy ya gyada kai yana murmushi yace "Su masu wayo wai, gaskiya ne ya kamata su kai ma Hansatu ziyara tunda gashi bata samu xuwa biki ba ba lafiya" Abba yace "In sha Allah I will see to that on Tuesday if everything is settled" Daddy yace "Alhmdllh, Allah ya kai mu lafiya" Washegari Friday bayan an sakko juma'ah aka daura auren Seeyama da angonta Abdul, throughout shagalgulan da ake a gidan imaan na dakinta tana bacci ko ankon bikin bata sa ba, Ammi bata takurata ta shiga jama'a ba sanin cewar bata wani jin dadi, kuma dama bata son tayi stressing kanta ta jogana masu wani ciwon, sai dab da xa a tafi da Amarya Ammi ta tasheta don tun daxu Inna ke cigiyarta, sai a sannan imaan ta shiga bayi tayi wanka ta wanke baki ta fito ta shirya cikin daya daga ankon da suka yi, ta d'an shafa powder tasa eye pencil da chappette, sannan ta dau farin hijab har kasa ta saka ta dau wayarta, ganin missed call ta tsaya ta duba, Sadeeq ne ya kirata, komawa tayi ta xauna tayi dialing, katsewa yyi ya kirata, bayan sun gaisa yace "Ina kika shiga yau" tayi murmushi tace "Bacci" yace "Uhm baki da damuwa, ya su mama?" Tace "Alhmdllh" yace "Daxu Mariya tace min kuna biki gidanku" tace "Ehh haka ne" yace "Shine ba gayyata?" Tace "Uhmm" yace "Toh kin kyauta" a hankali tace "Kayi hakuri, next time" yace "Toh waye next din auren? Ko ke?" Ta xaro ido sai kuma tayi dariya tace "Ni kuma, yar yarinya da ni" yace "Haba?" Tace "Ehh mana" yace "How old are you?" Ta langwabar da kai tace "Na kusa 19 soon" dariya yayi yace "Ehh gaskiya ne, ke yarinya ce sosai ma" tace "Toh kaga" yace "Ko aure aka maki yanxu ma baxa ki haihu ba ai" ta xaro ido sai dai bata ce komai ba tayi murmushi, yace "Yeahh" tace "Xa mu je raka Aunt dina dakinta yanxu" yace "Wani anguwa ne?" Tace "Ban sani ba dai" yace "Toh idan kun je gidan ki kirani" tace "Toh in sha Allah" sallama yayi mata ya katse wayar. Inna ce tsaye tsakar gida ta cakare cikin atamfa England an mata dinkin su irin na tsoffi, ga katon gyalenta ta yafa, ga mutane duk ana ta shirin xa a wuce da seeyama gidanta, motocin dake compound din sun fi shidda duk na daukan yan kai amarya, tun daga nisa Imaan ke jiyo Inna ta tana cewa "Naga abinda ya isheni bai ishi Allah ba, duk an wani yi cirko cirko a gaban motoci ku ja baya mana kar ku gurje masu dukiya in shiga uku, ni wllh saboda bala'in mata ma duk xafi ya isheni abu kamar maita dai, ke Maimuna ba ca nayi ki dubo min Imaan ba ko har yanxu jinin bai dauke ba ne, duk yau ban ganta cikin jama'ah ba ko bakin ciki take ma yar uwartata ban sani ba" Imaan ta turo baki bayan sun hada ido da Innar, inna ta ja tsaki tace "Kai ni dai ko limamin babban masallacin Habuja ne Bukar yau dai baxai hanaki sa gyale ba, duk yan uwanki ga su fess cikin gyale ke ko kin maka hijabi uwa xamu je xaman makoki ba amarya xa mu kai ba haba imaan, ni dai na gaji da maganar ki a gidan nan" Imaan ta dauke kai har ta iso gun motar, wata kawar Umma ce ta xo tayi announcing wai Umma tace wasu su fara tafiya kafin a fito da amarya, nan aka fara kokarin shiga motoci, inna ta bude baki ta gwalo ido ganin wata katuwa cikin shiga ta alfarma da gwalagwalai na kokarin shiga daya daga motocin, cikin daga murya tace "Wayyo meye wannan kuma... Kee don Allah ki bar sirara su shiga, banda neman magana da tsokanar fada ina xa a dake a haka, kisa kike son yi cikin motar fisabillahi, wannan ai sai dai idan ke kadai xa aje a ajiye a dawo to ina kuma hakan xai yiwu tunda motar ba taki bace, fito don Allah mutane su shiga" Imaan ta boye fuskarta da Hijab kar tayi dariya, mutanen wajen wasu sai dariya suke kasa kasa, matar ta fito kamar warce ruwa ya cinye kanta a kasa, inna ta karasa kusa da ita tana kallonta tace "Haba baiwar Allah... ke ba kya tsoron Allah ne wannan abu haka kinyi wani bake bake bayan motar mutane, ina kike son a xuba sauran jama'a, ko ke baki ga irin ki bane" Wata mata ta karaso kusa da Inna tayi kasa da murya tace "Hajiya babban kawar uwar amaryar ce fa" inna ta bude baki tace "Babban kawar uwar amarya kuma sai a sa mata ido ta latse hanjin 'ya yan mutane a bayan mota, dama kisan kai ya kawota ba biki ba, wannan abu kamar giwa kice ta shiga mota, amma bakya tsoron Allah wllh" sum sum matar ta bar wajen, Inna ta ja tsaki tace "Kai sirara su shiga a wuce, ba ruwana a aje a tatse hanjin mutane daga kai amarya ace bikin jikata ga abinda ya faru, to banda gwalagwalan ma duk karya ne ya xa ayi kamar ta ace bata da mota, ke kuma imaan ga motar da xa mu shiga can da Seeyama nace ban son tukin kowa sai na Mujaheed haka kawai mahaukatan abokan angon su ja mu su watsar da mu a rami" Bude motar Imaan tayi ta shiga back seat tana murmushi, Maimoon xata shiga inna tace "Toh ina kuma wancan figaggiyar xata shiga ni patuu, ba ga motoci can ba" Maimoon ta sauka da sauri, Imaan ta dinga dariya har da kyakyatawa, Kamar yanda inna tace Mujaheed ne ya ja su, ita, Seeyama da kawayenta biyu sai Imaan, suna hawa main road inna tace "Toh yau dai Seeyama gashi xa mu kai ki dakin ki, duk da dai mijin naki wani ga6o ga6o ne kiyi masa biyayya iya yanda xa ki iya, ni baxan ce kiyi hakuri yaje ya kashe mana ke ba gaskiya, bbu xancen xaman hakuri, mu dai da aka cuta da hakan aje a haka, amma duk kika ga abinda baxa ki iya dauka ba yafa gyalenki ki dawo gida, ko ki tafi sashin ubanki ko ki tafi sashin kaninsa ko kuma ki yo sashina sai iya Inda karfin mu ya kare na kwatar maki hakkin ki, ni fa tun daga lefen da ya hada maki dama na raina masa aji...." Mujaheed da takaici ya ishesa yace "Haba inna yanxu fada kike mata ko hudubar tsiya?" Inna ta hade rai tace "Ka ji min yaro da aka haifa ina tsaye bakin kofar asibiti daga safe har dare, kai xaka koya min xaman duniya Mujaheed, ko ance maka ban san abinda nake bane, to bari kaji ko kai yau aka daura ma aure iyakar abinda xan gaya ma matar kenan don ni yar gaskiya ce, akan me xa ayi ta wani ce ma mace tayi hakuri gidan miji ana cutarta ana musguna mata, Allah kadai yasan me yasa ya halitto ni a mutan da ba na yanxu ba, kuma ai bance kada tayi masa biyayya ba kawai idan taga xai takata ta gudo gida, ina laifin wannan shawara tawa??" Kawayen Seeyama dai sai kallon inna suke k'asa k'asa, inna ta ja tsaki tace "Tun da shaidan duk na makale gefen xuciyar ku ba dole kaji haushin abinda na fada ba, maxa dai sun xama masifa yanxu, duk halinku daya dama, yo banda halinku daya ya wuce idan yace xai walakanta maka kanwa ka matse gantalalle ka nakada masa duka tunda ga irin sa kamar tsinken sakace, wllh xaka iya dukansa" Seeyama dake hawaye cikin gyalenta ta fashe da dariya, imaan na taya ta, shi dai Mujaheed bai ce komai ba yana mamakin warce Allah ya basu matsayin kaka..... *The book Imaan is not free, you read for free ur cup of coffee wllh*🤷🏻‍♀️ It's 300 via Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah Then u show ur evidence of payment via my WhatsApp digit 07087865788 to be included in the payment group.Suna isa gidan bakin inna ya mutu murus sai 'yan idanuwa ganin gida ne ba na wasa ba, ni ko nace dama Umma ce xata yarda 'yar ta ta auri mai rufin asiri kawai?? Inna ta fito cikin motar tana cewa "Fito da kafar ki ta dama in sha Allah gidan xama ne, yi nayi bari na bari, aure kuma da kike gani d'an xaman hakuri ne duk shi muka yi muka kawo yanxu da rai da lafiya, Allah ya maki albarka yasa gidan ki ne ke kadai don na xauna da kishiyoyi ban ji da dadi ba, kishiya masifa ce" Wani kallo Mujaheed ya dinga mata, inna na washe hakora tana kara kallon katon gidan tace "Toh kai Mujaheed baka da abinda xaka ce mata ne ka tsaya wani sandandan kana kallonmu, wannan ai ya ma fi gidanka girma wllh" Yace "Kece baki mata nasihar tun a gida ba amma ni nayi tun a can" Kuka kawai Seeyama take, inna ta hade rau tace "Ji shashanci don Allah, to ki bude ido ki ga gidan mana idan ba sae kin daina shegen kukan nan ba" Mujaheed ya karasa kusa da ita yana kallonta yace "Be the best wife you can be lil sis, wishing you a peaceful married life" rungumesa tayi tana kuka, shi ko ya dinga kallon imaan da ta ja can gefe tana 6a66aka dariya har da rike ciki, ganin kallon da yake mata ta shige cikin gidan da sauri bata kuma fasa dariyar ba, cike da damuwa Inna tace "Ni dai wllh wannan 'ya ta Bukar gani nake kamar ciwace ciwacen ta ya shafi kwakwalwarta, to banda haka taya xa a kawo yar uwarki dakinta tana kuka, ke baki bata hakuri ba kina dariyar mugunta, to Allah dai ya kai mu naki kiga iskanci wllh" tana fadin haka ta janye seeyama tace "Mu shiga ciki kiyi kukan a tsanake kin ji jikalle, kai kuma Mujaheed bayan isha ka xo ka daukeni, idan kuma ya kama a nan xan kwana to shikenan" daga haka suka wuce ciki shi kuma ya fita compound din da motarsa yana girgixa kai. Bayan Magrib da rashin arxiki inna ta sallami duk kawayen Umma yan kawo amarya, Aunty da Ammi dama basu dade ba suka bar gidan, tsaye inna tayi bakin kofa rai bace tana cewa "Wannan ai ba yi bane, sai kace baku da maxaje baku da mafada, amarya dai ga ta an kawota lafiya har ta hakura ta daina kuka, to ai kuma sai kowa ya kama hanyar gidansa sai kuma wata shekarar idan ta haihu, amma duk kun wani ja6e ba niyyar tafiya, a dai dinga jin tsoron, ni ma nan da ku ka ga ban tafi ba kakar ta ce, ni na haifi ubanta Ahmadu, bai baci ba ko da cewa nayi xan kwana, amma mutane karere kawai ku cika gidan yarinya kun ki tafiya, ko ita Rukayyar ce tace ku kwana tare da su bani da labari? To ni dai ba ruwana" Wa enda suka fita iskanci yi suka yi kamar basu ji abinda take cewa ba, wasu kuma haushi yasa duk suka bar gidan, a fusace inna tace "Mata wasu katangala kawai rai ba ga ta sun xaune ma yarinya a gida, ni ban taba ganin haka ba tunda uwata ta haifeni, ku barta daga ita sai kawayenta su ma a xo a sallamesu su kama gabansu mana" Inna na kallon imaan dake kokarin fita ta gefenta tace "Ke kuma ina xaki sanyi ya kare maki ki cuci d'a na da kashe kudi?" Imaan ta turo baki tace "Ina xuwa ni dai" inna tace "Toh kar dai kiyi nisa don Mujaheed ya kusa xuwa yanxu, ba ruwana in kwana su Ahmadu su min fada" imaan bata ce komai ba ta fita, tana ganin motarsa ta gane don layin tamkar rana saboda hasken fitilu, ta karasa gun motar ya bude ya fito yana kallonta, Ta sunkuyar da kai tace "Ina yini" yace "Lafiya lau Imaan, nan ne gidan sistern naki?" Kai ta gyada masa, yace "Maa sha Allah, Allah ya basu zaman lafiya" tace "Ameen" yace "Amma ba nan xaki kwana ba dai koh?" Ta xaro ido tace "In kwana kuma?" Murmushi yyi ya rungume hannu sa yace "Shi na gani ai, Idan kika kwana ai xaki yi inconveniencing amarya da angon" turo baki tayi tace "Toh ni dama ta ya xan kwana" yar dariya yayi yace "Gaskiya ne, yaushe xa ku koma gida?" Tace "Muna jiran yaya ne, xai maida ni da Maimoon da Grandma dinmu" yace "Ohk yayanku kenan" ta gyada masa kai, yace "Idan bai taho ba let me drop you people mana" ta xaro ido tace "Bayan ma yana hanya yanxu, ai shi ya kawo mu" Yace "Ohk then...." Bata kuma cewa komai ba, shi kam yyi shiru yana kallonta, a hankali yace "Kin yi kyau" Dauke kai tayi tana murmushi, shi dai bai fasa kallonta ba, murya can ciki tace "Kai kuma baka sa glasses dinka yau ba" wara ido yyi yace "Ya 6ata.... sai dai ki siya min wani" ta kallesa tace "Da gaske?" Yana murmushin sa mai kyau yace "Yea" Sunkuyar da kanta tayi, yace "Ko baxa ki siya min ba" Ta d'an kallesa tace "Xan siya" yace "Toh yaushe xan xo amsa?" Tace "Idan na siya" yace "Toh gobe nake so, I can't do without it" da sauri ta kallesa sai kuma ta dauke kai tana murmushi tace "Toh Allah ya kai mu" yace "Ameen... Da yamma xan xo amsa" ta girgixa kai tace "A'a kawai ka bar shi next tomorrow" Shiru yyi yana kallon bayanta.... Can yace "Or wancan ne yayan naku?" Imaan ta juya da sauri taga motar Mujaheed yayi parking, ta gyada masa kai a hankali, tunda Mujaheed yyi parking d'an nesa da su dama yake kallonsu, Sadeeq yace "Tunda ya gan mu bari in je mu gaisa" shiru tayi da farko, ganin yanda yake kallonta a hankali tace "Is it necessary?" Yayi murmushi yace "Baki son yan gidanku su san ni kenan?" D'an bude ido tayi tace "Toh kaje ku gaisa ni xan shiga ciki in kira su Maimoon" yace "Ohk" gate ta nufa tana satan kallon Mujaheed da ya bi ta da kallo gabanta na faduwa, Sadeeq kuma ya nufesa, sauke glass Mujaheed yyi ya bude motar ganin sadeeq, ya fito yana kallonsa directly cikin ido, sadeeq ya masa sallama hade da mika masa hannu, sai bayan kusan seconds biyar Mujaheed ya mika masa nasa yana d'an murmushi wanda iyakarsa lips, nan suka gaisa... Cikin cool voice Sadeeq yace "I am Dr Abubakar Ahmad" Mujaheed ya gyada masa kai kamar baxae ce komai ba, sai kuma yace "Muhammad Ahmad" Sadeeq yace "Maa sha Allah it's nice meeting you" Mujaheed yace "Same" Sadeeq yace "Alryt xan koma, sae da safe" Mujaheed yace "Ohk... kun yi sallama ne" Sadeeq yace "Sure" daga haka ya nufi motarsa ya shiga ya wuce. Inna bata fito parlon Seeyama ba sai da ta kada kan sauran mutanen dake parlorn, har Mujaheed ya gaji da jira cikin mota, Inna ta fito gate tare da Maimoon da Imaan ta shiga bayan mota tana cewa "Mujaheed kaga Gantalallu kila da so suka yi su kwana a gidan, don da ban masu jan ido ba baxa su tafi ba, ni dai ba ruwana" Maimoon ta bude front seat ta shiga, imaan ta shiga back seat gun inna, Mujaheed dai bai kulata ba yyi reverse, Inna tace "Ni bikin Imaan da na Maimoon ma gaskiya sae na xabi wa enda xa su raka su daki, iyaka kawai in xauna bayan mota ni da su don ina fatan ya xamo rana daya, Mujaheed ya ja mu in kai su dakunan su ya maida ni gida idan Allah ya yarda, ba katuwar da xata bi mu" Mujaheed dai driving yake har ya bar layin ya hau saman titi, lkci lkci ta madubi yana kallon imaan da ta ki yarda ta kalli gaban motar, inna tace "Mujaheed kaga kawayen uwar ka kamar mayu kuwa, wllh da kyar na kora su, duk sun ban wahala, ita ina ta samo su haka wasu lafta laftan mata ba kyan gani kamar aladu? kaii Rukayya dai shahararriyar mahaukaciya ce wllh" taka brake Mujaheed yyi bayan ya tabbatar bbu motar dake bayansa ya gangara gefen titi, inna ta saki salati tace "Lafiya Mujaheed, me ya sami motar" ya bude motar ya fita ya bude side dinta yana kallonta yace "Ita uwar tawa ce mahaukaciya?" inna ta bude baki tana kallonsa, sai kuma ta kalli Imaan tace "Ga reshen bishiya can, sauka ki karyo ki kawo masa...." Imaan ta hade kai da kafarta tana dariya kasa kasa, a fusace inna ta kunduma masa xagi tace "Na ce mata mahaukaciyar sharri na mata, da hankalinta ina ita ina gunduma gunduman matan da ta ajiye matsayin kawaye, wasun su idan suka xaune kanta shegiya nake idan bata suma ba bayan sun latse ta" yace "Ku saukar min a mota ku samu wanda xai kai ku gida Hajiya" kamar jira Inna take ta sauka da sauri tana kallon Imaan tace "In dai kin san motar ba ta Bukar bace ki sakko ki bar masa tsiyar sa" Imaan ta hade rai tace "Inna bai ce har da mu ba fa" Irin kallon da Mujaheed yyi mata yasa ta sauka da sauri don ya dade bai mata irin kallon ba, Inna ta kalli Maimoon tace "Ke kuma idan ba ta Amina bace motar ki sakko kema" Maimoon ta bude front seat ta sakko, inna ta fara matsar kwalla tace "Ku sama min Adaidaita sahu" ko kallonta Mujaheed bai yi ba ya rufe back seat dinsa ya shige motarsa ya kara gaba, inna ta bi motar da kallo tace "Allah dai ya isa, kuma sai Ahmadu ya min iyaka da Mujaheed yau, ni xai toxarta ya walakanta a bakin titi a kan Rukayya" Imaan ta tsayar da adaidaita ta fada masa inda xai kai su, Mai adaidaita yace "Ba can xan yi ba" bai gama rufe baki ba inna ta shige adaidaitan ta xauna, Imaan da Maimoon suka saki baki suna kallonta, Mai napep din ya juya yana kallonta yace "Baaba nace ba can nayi ba" a fusace tace "Dalla can mu je d'an nan, ko baka ganin dare yyi ne xaka ce min ba can kayi ba, jika na ne fa ya watsar da mu a titi yanxun nan yyi wucewarsa daga nayi ma katuwar uwarsa gyara, banda haka yaushe xaka gan ni bakin titi tsaye da gata na, motocin 'ya yana sun fi biyar wllh, ko da yake in mun je gidan ma xaka gane abinda nake nufi, ko kai so kake inyi ta tsayuwa kamar yar iska bakin titi?" Shiru yyi bai ce komai ba, Inna ta kalli su Imaan sannan ta kallesa tace "Yaro idan baxa su shiga ba ja ni ka kai ni gida, su kuma Allah ya kawo masu mafita, mu je ni dai" murmushi mai napep din yyi, Imaan ta turo baki ta shiga Maimoon ma ta shiga, inna tace "Atoh da kun tsaya jiran d'an sahun da xai je ku kwana a wajen" suna isa gida dama inna ta sauka napep din ta nufi gate tana gyara yafin mayafinta, Maimoon ta kalli Imaan dake dariya ta ja tsaki ta bude jakarta ta fiddo dubu daya ta basa ya bata canji ta wuce ciki, can suka ga inna har ta shige parlon su Maimoon, Imaan ta nufi part din su Maimoon ta bi bayan Inna, babu kowa parlon Abba hakan yasa inna ta dawo main parlor tana kallon mutanen da ta wuce da farko tace "Ahmadu baya nan ne" Daga kitchen Aunty ta leko tace "Bai shigo ba inna, kun dawo lafiya?" inna bata tanka ta ba ta fice parlon, bata tsaya ko ina ba sai part din su Imaan, ba kowa parlon sai kamshi dake ta tashi, cikin daga murya inna tace "Salama alaikum" Imaan ta bude kofar bedroom dinta tana lekowa, Inna tace "Ina Bukar din?" Daddy ya fito daga daki yace "Har kun dawo inna" karasawa cikin parlon tayi ko takalmanta bata cire ba ta xauna saman kujera tana share guntun hawayen idonta, Ammi dama na jin irin sallamar da inna tayi tasan ba lafiya don haka bata fito ba, duk xaton ta k'aran imaan ta kawo, Imaan da har ta cire kayanta ta sa Hijab kawai ta fito da sauri, Daddy na kallon inna a hankali yace "In ji dai lafiya inna" a fusace tace "Ina fa lafiya Bukar, shegen d'an ku ya watsar da ni tsakiyar titi gefen jaji yayi wucewarsa, daga nayi ma Rukayya gyara" Shiru Daddy yyi yana kallonta da mamaki, ta fashe da kuka tace "Gaskiya Bukar idan ba a bi min hakkina ba yau duk a station xa mu kwana gwara in kai karar can a bi min hakkina, da girmana da matsayina da martabata Mujaheed xai juye ni tsakar titi yyi wucewarsa?? Ae wannan babban magana ce wllh" Daddy ya sauke ajiyar xuciya yace "Subhanallah me ke damun Mujaheed haka" Inna ta tsaida kukan da take tace "Toh ai ba ni xaka ma tambayar ba, waya xaka dauka yanxu ka kirasa, kada ma ka nuna masa ina nan, kawai ce masa xaka yi ya xo xaka aikesa yanxun nan, daga nan sai kaji me ke damunsa ko wiwi ya fara sha bamu sani ba" Daddy ya kara sauke ajiyar xuciya, inna tace "Sae wani sauke sauken ajiyar xuciya kake Bukar, ko tsoron sa kake ne inyi ta kai na?" Yar dariya kawai daddy yayi ya dau wayarsa, inna ta tsuke fuska tace "Wllh yanda ya min tijara a kan uwarsa kai ma haka xaka masa tijara akan taka uwar, kuma idan baka ce masa aikensa xaka yi ba wllh baxai xo ba nan kuma xa mu kwasa mu tafi police station " Daddy dai bai ce komai ba yayi dialing number Mujaheed ba a dau lkci yana ringing ba ya daga, Daddy yace "Muhammad kana kusa ne?" Daga daya bangaren Mujaheed yace "Eh Abba" daddy yace "Toh ka xo parlor na yanxu" Mujaheed ya d'an yi shiru, kafin yace "Toh Abba" Daddy yace "Don't keep me waiting fa naji kayi shiru ko baka kusa ne?" Yace "Ina nan" Daddy yace "To ina xaune ina jiranka yanxu" Mujaheed yace "Toh" daga haka daddy ya katse wayar, inna tace "Kai xaka kwana a ciki wllh idan yaron nan bai xo ba Bukar" Daddy dai bai ce komai ba, Mujaheed ba don yanda yake jin kunyar daddy ba da fa ba xai je ba don yasan sarai inna na can, kuma da Abbansa ne ma ya kirasa ba lallai yaje ba, jallabiyarsa kawai ya xura ya fita dakinsa, banda girgixa kafa babu abinda inna take, da sallama ya shiga parlon, ba tare da ya kalli Daddy ko ita ba ya tafi ya xauna kasan lallausan carpet din parlon yace "Barka da dare Abba" Daddy yace "What happened between you and ur grandma yanxu?" Mujaheed ya daga kai yana kallonta yaga yanda ta wani tsuke fuska tana kallon sa, ya maida kansa kasa, inna na nuna Imaan dake kwance kan kujera tana kallonsu tace "Idan sharri na masa ga 'yar ka kwance kusa da kai ka tambayeta ka ji ko ba tsakiyar titi ya juye mu ba" Daddy ya juya ya kalli Imaan, a fusace Inna tace "Ke tashi xaune ki basa labarin abinda ya faru, ba tsakiyar titi Mujaheed ya sauke mu ba, naga kamar tantama Bukar yake" Imaan ta mike xaune tace "A'a ba fa tsakiyar titi bane inna, gefen hanya ne....." Rai bace Inna tace "Amma wannan anyi shegiyar 'ya... Dama akwai bambanci tsakanin gefen titi da tsakar titi, ke dai munafuka ce wllh" Imaan ta harareta ta gefen ido tana turo baki ta koma ta kwanta, Inna tace "Wllh Bukar gefen hanya yayi watsi damu, kuma kafin ya sauke ni don Allah mai yace min Imaan" da sauri Imaan ta daga hannu tace "A'a ba ruwana nima ban sani ba" Bude baki inna tayi tana kallonta, daddy yace "Yanxu dai ki tashi ki tafi ki bar ni da shi inna" inna tace "In tashi in tafi ka basa hakuri shima ya tafi xaka ce min" Tana fadin haka ta mike tace "Tun farko ma ban san me ya kawo ni gun Bukar ba, duk inda Ubansa ya tafi ai ya ci ace ya dawo yanxu" daga haka ta fice parlon fuska daure. Daddy ya hade rai yana kallon Mujaheed yace "Saboda baka da kirki xaka ajiye su bakin hanya Muhammad?" Mujaheed yyi kasa da kai bai ce komai ba, Daddy yace "Yanxu ka kyauta kenan, idan Hajiyar ka ce ko min abinda tayi maka xaka mata haka?" Yace "Kayi hakuri Abba" Daddy yace "Haba Muhammad, I am highly disappointed at you, this is very rude and stupid of you, she is our mother fa, no matter how she behaves baxa mu canxa ta ba" Mujaheed bai iya cewa komai ba, daddy yace "Ka tashi ka bi ta ka bata hakuri yanxu" yace "Toh, ayi hakuri Abba" Daddy ya kalli imaan yace "Ke kuma I've warned you times without number ki daina fada mata magana anyhow amma baki ji ko, xan fara sa6a maki soon wllh idan baxa ki canxa naughty attitude din nan ba, will you dare talk to ur mother that way?" mikewa xaune tayi kamar xata yi kuka, Mujaheed ya tashi yace "Xan je in sameta yanxu Abba" daga haka ya fita parlon. Washegari da safe da kyar imaan ta tashi tayi wanka tayi breakfast da Ammi ta ajiye mata a dinning, Ammi tace "Idan kin gama ki dau magungunanki ki sha kada in tuna maki, kuma da Ac kika kwana ko?" Ta xaro ido tace "Ammi wllh A'a" Ammi tace "Toh ga mura nan na shirin kama ki" Ta langwabar da kai tace "Jiya fa da daddare a napep muka dawo, kin ji sanyi kamar xanyi freeze a hanya" Ammi ta fiddo kindirmo a fridge yayi sanyi sosai ta ajiye mata a dinning din tace "Gashi ki kai ma inna inji daddyn ki, you make sure kin goge min dinning table idan yayi stain" Ta marairaice tace "Ammi my legs are aching me fa" Ammi ta harareta ta wuce dakin ta, Imaan na gama breakfast ta tashi ta dau kindirmon ta tafi kai ma inna, Tana shiga parlon bayan ta ajiye tana kallon inna dake ta kukkula dubulan da cin cin a leda sai ga Umma ta shigo parlon da sallama, Inna ta kalleta ta ci gaba da abinda take ta amsa sallaman ba yabo ba fallasa, Umma ta dafa kujera tace "Ina kwana inna" inna tace "Lafiya lau" Umma tace "Ya gajiyan taro" inna tace "Bana tare da gajiya duk ya bi lafiyar gado" Umma tace "Toh Alhmdllh Allah ya saka da alkhairi yaji k'an mahaifa" inna tace "Ameen" karasawa tayi kusa da inna ta ajiye ledan hannunta tace "Ga wannan dai ba yawa" inna na kallon ledan tace "Meye wannan din? Ke imaan xo ki bude" imaan dake xaune ta mike ta karasa kusa da Inna, Umma ta bi ta da kallon gefen ido, durkusawa tayi ta bude ledan ta ciro atamfa da pack din sabulu guda biyu da turare mai tsada" Inna ta bude atamfar tana kallo da kyau, tace "Holland ce wannan din?" Umma tace "Ehh" inna ta tabe baki tace "Toh, da dai basirar ki ce hakan da sai ince Allah yyi albarka, amma wannan ko kaffara baxan yi ba Ahmadu ya sa ki, Allah ya masa albarka ya kare min shi duk inda xai shiga, Allah ya ci gaba da hada kansu da d'an uwansa Bukar ya raya mai 'ya yansa yayi masu albarka, ita kuma wannan da ya aurar Allah xaunar da ita da mijinta lfya, ke kuma nagode da isar da sako" Umma ta dinga kallonta ko kiftawa babu, Imaan sai danne dariyarta take, Inna ta ci gaba da kulla dubulan dinta a leda, Umma tace "Sai anjima" inna tace "Mu jima da yawa" daga haka ta nufi kofa, inna na kallon Imaan tace "To ke sai kiyi ta kanki, don wllh jiya Mujaheed ce min yyi xai kakkarya ki ya xane ki, wai ya ganki da wani mai mota a tsaye a kofar gidan seeyama, imaan ina kuma kika samo mai mota kike ta boye min ban sani ba ni Asabe??" Umma ta d'an dakata bakin kofa jin abinda inna ke cewa, Imaan ta turo baki tace "Shi sa ma xan tashi in tafi yanxu kar ya xo nan, to har kun shirya ne inna?" Inna tace "Haba dai sai kace wata yarinya, to me yyi min da baxa mu shirya ba, wai na ce ma Rukayya mahaukaciya, ke ki ji fa? to me ta min xan xageta banda abunsa ma dai, kawai daga ina mata gyara? Ni fa na yarje ma Ahmadu ya aureta wllh, baki ganta ba a lkcn yar siririya yanda kika ganki, kamar iska xai hure 'yar banxa ta fadi, gashi iyayenta basu da komai basu kuma ba wani ajiya ba, wani d'an akurkin gida fa gare ubanta a lkcn, to ni ban masu bakin ciki ba don xuciya ta fess mai kyau ne na yarda Ahmadu ya auro mana ita a haka, ke kinga wahalar da nayi da ita kuwa? Wllh kare baxai ci ba, gashi ba abinda ta iya a lkcn, har girki ni ke sa ta kan hanya ina koya mata, kishiyoyina su yi ta jin haushi yanda nake ji da ita bana son ko k'uda ya ta6ata har dai ta samu cikin wannan yaro Mujaheed, sai kin ga wahalar da nayi mata sbda laulayin da ta dinga yi ba kakkautawa, to ni duk ba wannan ba don nasan sakayya ta dai na gun Allah, to don kuma yanxu Rukayya ta xama abinda ta xama sai me xai dameni ni patuu? ga dai Amina na bina sau da kafa ga Aisha, ni dai abinda na sani shine Mujaheed ai xai yi auren, to nan xata d'an dana ko da dadi ko babu, abinda duk abinda ka shuka shi xa ka girba, tsaf xan karance ma yarinyar xaman da xata yi da ita, muna nan da ku sai an dinga xuwa daukata shari'a a mota...." Imaan har wani kwanciya tayi kan kujera tana dariya amma ba mai sauti ba, Umma da ta makale jikin kofa ta fita ta sa takalmanta, inna ta tabe baki tace "Wllh Mujaheed da gwiwowinsa bibbiyu ya durkusa ya dinga ban hakuri tun ban kai ga gaya ma ubansa ba, to tunda naga yyi nadama kawai sai na yafe masa don ba halinsa bane gaskiya bai taba juye ni a tsakiyar titi ba tunda mu ke" Imaan ta fashe da dariya tace "Jiya dai ya juye ki ai" *,Umma na komawa bangarensu kallo daya tayi ma Mujaheed dake xaune dinning yana shan coffee tace "Ka sameni daki yanxu" sosai gabansa ya fadi ya bi ta da kallo har ta haura sama, bai iya ya karasa shanye coffee din ba ya mike ya bi bayan ta, tsaye ya ganta tana safa da marwa a dakin, Yace "Gani Umma" ta juya tana kallonsa fuska daure tace "Mujaheed ina son sanin meye matsalar ka don kaga shegiyar yarinyar nan da mai mota jiya har kake ikirarin hukuntata" ya xaro ido yace "Ban gane ba Umma" Ta masa wani mugun kallo tace "Bana son ka gane dama ai, warce kaje ka ba sakon take fadi yanxu naji, dama baka raba kanka da makiyan nan nawa ba har ynxu Mujaheed? Mujaheed ka gaya min meye hadin ka da yarinyar nan Imaan?" Yace "Haba Umma, ke yanxu maganar inna kike dauka, kila ma don ta ganki yasa ta kirkiri haka, ni a ina na ganta har muka yi wannan xancen da ita?" Shiru Umma tayi tana kallonsa, a ranta kuwa tunani take kila hakan ne ma, ganin Umma tayi surrender, Mujaheed yace "Kawai ta fada haka ne don ki sa a rai, ni yaushe nake da wannan lokacin ma a gidan nan yanxu" Umma ta sauke ajiyar xuciya tace "Sae ma kaga rashin mutuncin da ta min kayan da na kai mata, ni na ma ji dadin da ta gane cewar in don ta nine baxan bata ko tsinke na ba, basirar Abban ku ne kamar yanda ta fada" Mujaheed yyi murmushi bai ce komai ba, Umma tace "Gobe xan baka sako ka kai ma Hajiya Mansura ta marafa, bata samu xuwa bikin ba amma ta bada gudunmawarta dubu dari, cin cin da su alkaki xaka kai mata daga nan nasan xa ku hadu da Safeenah, tana nan ba ta koma makaranta ba, ni so nake nan da 'yan watanni a fara xancen naka bikin" shi dai Mujaheed bai ce komai ba banda kallonta da yake, ta xauna gefen gado tace "Kar fa kace min ka manta gobe kayi ficewarka, xuwa sha biyu in sha Allah xaka kai masu, tunda gobe lahadi" ya shafa kai yace "Allah ya kai mu" daga haka ya nufi kofa ya fita. Imaan ta kara leka samirar dake cike da cin cin da dubulan da alkaki da inna ta basu su kai ma ta rasulu aminiyarta, ta tabe baki tace "Wllh duk kin kwashe ma tsohuwar, mu fa har ynxu ba mu ci ba" inna ta tsuke fuska tace "To ina ruwana da rashin cin ku, ni na aurar da 'ya ko ko? Kaji min dai, Dubu talatin ta rasulu ta bada a kawo min gudunmawa, kuma ace baxan cika mata samira da kayan flawa ba, ni ta ma fi min Aisha kiji in gaya maki" Imaan tace "Kice ma ta fi maki har daddy mana" Maimoon tace "Toh ina dubu talatin din?" Inna ta kalleta da sauri tace "Amina aka ce in ba wa da xaki tambayeni dubu talatin Maimuna? Ko ko kin ban ajiya ne? Ni dai ku daina sa min ido a gidan nan, idan ba haka ba mugun alkaba'i ba shi da kyau amma to xance kowa ya ci kansa gaskiya" Imaan ta kalli Maimoon tace "Maimoon karbo kudin motar mu wuce" Inna ta kunce ha6ar xaninta ta fiddo naira dari ta ajiye masu tace "Hamsin xai kai ku ya dawo da ku, nan nan kabala dai" Imaan ta ajiye samirar ta xauna tace "Tabdi ko naira dari dari ma baxa a yarda a kai mu ba balle hamsin" Inna tace "Barawo ne mai adaidaitan da baxai kai ku a hamsin ba, ko ya sha wiwi ne, wllh kullum a hamsin ake kai ni a dawo da ni" Maimoon tace "Saboda ke tsohuwa ce ai" A fusace inna tace "Oh oh Allah, idan baxa ku ba ku ajiye min kayana ku fita, Xan kira Bukar ko Ahmadu cikinsu wani ya kai mun, ku fitar min a parlor" Kin fita suka yi jin abinda tace wai xata kira daddy ko Abba, Maimoon tace "Toh wai don Allah mu muka siya masu adaidaitan da xasu kai mu a hamsin su dawo da mu a haka, ki kara mana kudin mu tafi mana" Inna ta jefa masu wani hamsin tace "Aniyar ku ta bi ku dai" Maimoon ta dau kudin tana gunguni tace "Ae sai dai mu cika da kudin mu" Imaan ta tabe baki ta dau samirar tace "Sai dai ke ki cika, sisina baxan kara a kai ba tunda ba ni xan ci cin cin ba" daga haka ta fice parlon, inna tace "Shi sa har yau aka kasa gano cutar da ta sa ki gaba, saboda mugun xuciyar ki da rashin kunya, ni dai Allah ya saka ma d'ana, Allah ya saka masa kan kudaden da yake kashewa a kan tsadadden ciwon nan naki, Allah kuma ya raba shi dake lafiya, ya aurar dake ya huta ma ransa mijin ma ya d'and'ana ukubar, ba a taba jin alkhairi ya fito bakin ki sai sharri, to meye kuma don kin cika kudin mota" Maimoon ta bi bayan imaan ta kullo mata kofarta tana turo baki. Suna tsaye bakin titi suna jiran adai daita da xai je kabala, Imaan tace "Ko da yake nasan tsohuwar da xa mu kai ma baxa ta bar mu haka nan ba, kila ta ba mu kudin mota" Maimoon tace "Wllh da ba dan Abba da tace xata kira ya kai ba ba inda xanje ni dai, kullum fa idan xata aiki mutum sai ta raba kudin motar xuwa wajen kashi uku ta baka daya" Imaan tayi dariya tace "Kawai so take ayi ta mana fada shi sa tace xata aiki daddy ko Abba" motar Mujaheed da suka gani yasa suka yi shiru suna kallon motar, shi ma daga gida ya fito, ya sauke glass yana kallon Maimoon, Maimoon ta marairaice tace "Ya M.A inna ce ta aike mu kabala kuma ba mu samu adai daita ba har ynxu..." Ya gyada kai yace "Toh Allah ya kawo adai daitan" xai dage glass da sauri tace "Wait... Kai ina xaka plss?" Yace "Marafa" tace "Toh ka rage mana hanya mana don Allah" ya mata wani kallo yace "Me ya hada Marafa da kabala?" Tace "Yaya ai duk hanya ce mu dai ko ina ma ka ajiye mu nasan xa mu samu a can gaba" yace "Toh shiga" Imaan ta bude back seat ta shiga ya dinga hararanta ta madubi fuska daure, dama tun da suka hada ido taga kallon da yake mata bata sake yarda ta kalli madubin ba, Maimoon na kallon fancy nylon dake gaban motar ta dauka tace "Ya M.A wa xaka kai ma cin cin da dubulan?" Yace "Anty" dariya tayi bata sake cewa komai ba, sai da suka yi nisa yace "Gidan Baaba ta rasulu xa ki kenan?" Tace "Xa mu dai, ai ba ni kadai bace, ni da Imaan ce" ya watsa mata wani kallo ta xaro ido tana yar dariya ta rufe bakinta, har kofar gidan aminiyar inna ya kai su, Maimoon sai murna take tace "Ya M.A mun gode, ko mu raka ka marafan mu ma?" Shiru ya d'an yi da farko yana shafa kansa a hankali, lkci daya yace "Toh kar ki dade a ciki idan ba haka ba inyi wucewata" bude motar tayi ta fita tana kallon Imaan da ta fita tuntuni tana cinno baki suka shiga gidan, dari biyar ta rasulu dake ta sa masu albarka ta basu kudin mota, tace "Ina gaida Hajiya Asaben, kuyi mata godiya sosai, ita kuma amarya Allah ya basu xaman lafiya da mijinta, ku kuma Allah ya maku albarka ya fiddo maku maxaje na gari" suka amsa mata da Ameen, sannan suka mata sallama suka fita da samirar don juye kayan ciki tayi a nata samiran. Maimoon na kallon imaan tace "Wai Imaan me yasa baki gaida ya Mujaheed yanxu?" Imaan tace "Saboda baya gaida Ammi na sai ya ga Daddy" Maimoon ta xaro ido tace "Da gaske?" Imaan tace "Ehh mana" Maimoon tace "Toh saboda me" imaan tace "Oho" bude back seat tayi ta shiga Maimoon ta shiga gaba ya tada motar yayi reverse ya bar anguwar. Tafiyar kusan minti sha biyar suka yi suka iso gidan Hajiyan Marafa, Dai dai gidan yayi parking daga kusa da flowers yana kallon Maimoon yace "Xan yi sllh kafin in shigo" ya mika mata ledan yace "You take this in with you" tace "Amma yaya bamu san kowa a gidan ba fa" yace "Sai ki ce Hajiya ce ta aiko ki, ina nan shigowa nace idan nayi sllh" daga haka ya fita motar, Imaan dai na tsaye ta rungume hannu jikin motar bayan ta fita, Maimoon ta fito ya kulle motarsa da lock, ya wuce masallacin da ya gani a layin, Maimoon ta kalli Imaan tace "Mu je" bin bayan ta Imaan tayi suka shiga gidan, bayan sun sanar da mai gadi gun Hajiya suka xo, duk girman gidansu haka suka saki suke kallon gidan, Maimoon tace "Ni dai baxan shiga ba gwara mu jira sa a nan, kawai mutum yaje yana ta introduction ana masa wani kallo" Imaan ta yi dariya tace "Sai kice Hajiya Rukayya ce ta aiko mu" Maimoon ta buda ido tace "Bari ya Mujaheed ya jiki, wai Hajiya Rukayya" Imaan ta tabe baki suka shiga babban balcony din dake dauke da kujeru sannan ga babban rug a shimfide kasa, kan rug din suka xauna suna kara k'are ma gidan kallo, sai bayan da aka idar da sallah Mujaheed ya shigo gidan, kallonsu ya tsaya yi ya hade rai yace "What did I tell you Maimoon?" Ta marairaice tace "Yayanmu mun yi sallama kamar basa parlor" hararanta ya dinga yi kafin ya danna bell, ko minti daya ba ayi ba mai aiki ta bude kofar, ta gaishesa ya amsa yace "Hajiya tana nan?" Tace "Wa xa ace mata" Yace "Dr Muhd, Kice Hajiya Rukayya ce ta bada sako a kai mata" Murya can kasa Imaan tace "Toh ba gashi shi ma cewa yayi Hajiya Rukayya ba" Maimoon ta yi murmushi bata dai ce komai ba, Mai aikin tace "Toh ka shigo" bin bayan ta yayi xuwa cikin parlon da sauri imaan ta mike ta bi bayansa, Maimoon na yar dariya ta tashi ita ma ta shiga parlon, wata yarinya da baxata wuce ashirin da daya bace ta shigo parlon daga dinning kallo daya tayi masu ta wuce sama, tsaki imaan ta ja Mujaheed ya kalleta ta cinno baki ta dauke kai, mai aikin ta kawo masu drinks da bottle water ta ajiye, bayan wani lkci sai ga Hajiyar ta sakko cikin shiga ta alfarma ganin Mujaheed tace "A'a ashe kai ne doctor" yyi kasa da kai yace "Ina yini Hajiya" tace "Lafiya Alhmdllh, ya Hajiya Rukayyar, fatan an watse taro lafiya" yace "Alhmdllh" xaunawa tayi tana kallo su Maimoon da Imaan dake gasiheta tace "Wannan kamar kanwar khadijah da tayi aure Us koh?" Ta fadi haka tana nuna Maimoon, Mujaheed yace "Ehh kanwarta ce" tace "Maa sha Allah ga kamanni na gani, to ita wannan fa" Mujaheed ya kalli Imaan da ta nuna, da sauri yace "Yar uwarsu ce" tace "Allah sarki shi sa ban santa ba" Maimoon ta mike ta ajiye abun hannunta kusa da ita tace "Gashi Hajiya tace a kawo maki" Hajiyar tace "To maa sha Allah, nagode kwarai Allah ya basu xaman lafiya" Bude kofar parlon aka yi, wata yarinya ta shigo parlon cikin English wear bata ko kalli wa enda ke xaune parlon ba xata wuce sama Hajiya tace "Safeenah lafiya na ga ranki a bace" Jin sunan da Hajiyar ta kira Mujaheed ya daga kai yana kallon yarinyar, ita ba doguwa ba kuma ba gajera ba, farin ta har yayi yawa and she is beautiful, lkci daya ya dauke kansa, Maimoon da Imaan kuwa kamar sun samu TV imaan har da juyawa gaba daya tana facing dinta, rai bace Safeenar tace "Wai ki ji mum ashe birthday din ma wani local waje xa ayi, sai kinga yanda raina ya bace bayan duk shirin da nayi, wllh Saleema koluwa ce I don't know what's wrong with her, ni ko gaya masu na tafi ma ban yi ba" Mujaheed dai sai danna wayarsa yake, Hajiya tace "Atoh gaskiya basu kyauta ba, to why not baki ce masu a canxa hall din ba, ko ke ba sai ki biya kudin hall din ba" Tsaki Safeenah tayi tace "Ni duk raina ya baci wllh Mumy" xata wuce sama Hajiya tace "Toh ga doctor ku gaisa" Juyowa tayi tana kallon cikin parlon taga Mujaheed da ya ki dago kansa, ta fi second goma tana kallonsa, kafin ta karasa cikin parlon ta xauna hannun armchair da uwarta ke xaune cikin sanyayyen murya tace "Ina yini" sai a sannan ya daga kai yace "Lafiya lau, ya kike?" Tayi wani sanyayyen murmushi tace "Lafiya lau" Ta kalli su Imaan tace "Sannun ku" Imaan dai tace "Yauwa" Maimoon kuma ta gaisheta, Hajiya ta kwalo ma mai aiki kira ta fito da sauri, Tana kallonta tace "Pepper chicken da ku ka yi daxu xa ki kawo masu tun da ba ku gama lunch ba" Mujaheed yace "Daga gida muke yanxu Hajiya, we ate before leaving, so we are okay" tun da ya fara magana Safeenah ke kallonsa ko kiftawa babu har ya dasa aya, Hajiya tace "Wannan ae is more or less a dessert, daxu yara suka ce suna son pepper chicken, shine nasa su yi, kuma da yawa sosai suka yi don nasan baxa a cinye gaba daya yau ba sai dai a ba masu gadi da almajirai" Mujaheed ya d'an yi murmushi yace "Ni dai I am okay" Imaan tace "Ni dai xan ci" kallonta yyi da sauri, Hajiya tace "Yauwa, bar sa yayi ta fulako dama yayi kama da fulanawan, ke ma ai xa ki ci ko" Hajiya ta fadi tana kallon Maimoon, Murmushi kawai Maimoon tayi ta sunkuyar da kanta, mai aiki ta dawo rike da tray da plates uku a kai, ko wanne dauke da kaxa da aka yi garnishing sai kamshi da turiri yake, Mikewa Safeenah tayi ta dau plate daya ta karasa kusa da Mujaheed ta ajiye masa, hada ido suka yi yace "I said I am okay baxan ci ba" tace "Kaci ko kadan ne pls" Daga haka ta koma ta xauna, a hankali Imaan ta xamo kasa ta fara cin kazar, sai kallonta Mujaheed yake ta gefen ido, Maimoon ta dau tsoka daya daga kan kujerar tana ci a kunyace, Hajiya tace "To ya aikin doctor, Hajiya Rukayya tace min ka dawo Kaduna da aiki gaba daya yanxu koh?" Yace "Ehh" tace "To da kyau, Allah yayi albarka" yace "Ameen" idonsa na kan wayarsa amma da ya dago sai yaga kallonsa Safeenah take, Hajiya ta mike tace "Toh bari in d'an shiga ciki...." Mikewa yyi da sauri yace "Wucewa xa mu yi ai, xan je gun aiki" tace "Da wuri wuri haka, ka dai ki shan ko ruwa ne kuma ban ji ddi ba" yace "Am sorry bana jin cin komai ne yanxu" Tace "Toh ai sai ka jira kanninka su gama tukun na ko?" Yace "Bana son in makara xuwa gun aiki ne Hajiya" tace "Toh shikenan, bari a masu take away da shi" Imaan tace "Toh" wani kallo Mujaheed ya dinga mata, Hajiya ta kwalo ma mai aiki kira ta sanar da ita tayi masu takeaway din kajin, Imaan ta mike tace "Ina xan wanke hannu" Safeenah ta nuna mata hanyar dinning ko kitchen, tare suka tafi da Maimoon suka wanke hannu suka dawo, Hajiya ta basu dubu biyar Maimoon ta amsa da kyar, tuni Mujaheed ya fice gidan suka bi bayansa, Hajiya ta kalli Safeenah tace "Baxa ki raka su ba" bin bayan su tayi ita ma. Mujaheed har ya shiga mota sai ga ta tare da su Maimoon, tana kallonsa tace "I don't even know ur name" ba tare da ya kalleta ba yace "I am Mujaheed" tace "That's nyc, I am Safeenah" kai kawai ya gyada mata, Tace "Toh sai yaushe?" Yace "Watarana" yar siririyar dariya tayi tace "Do you mind sharing your digit with me pls?" Yace "Ohk" mika masa wayar hannunta tayi ya amsa ya sa mata lambarsa da bai fiye amfani da ba ya mika mata, tace "Thank you" yace "You are welcm" Daga haka ya tada motarsa ya wuce, haka ta bi motar da kallo har ya fita layin, da sauri ta koma ciki tana kallon uwarta tace "Wllh Mum naji ina son sa sosai" Uwar tace "Haba, to ai shine wanda na maki magana a kai kwanaki kika ce ke ba ruwan ki da hade hade in rabu da ke, uwarsa ce dama ta kawo shawarar ba ni ba tunda nasan kina da samari iri iri" ta marairace tace "Mum ai ban san haka yake ba, ni wllh mum ina son sa har raina" Hajiya tace "To ai shikenan, bari anjima sai in kira mahaifiyar tasa dama kwanaki duk ta dameni da kira a kan hakan bana daukan kiranta" Safeenah ta sauke ajiyar xuciya ta xauna tace "kaiii... Ya hadu wllh, his beards are damn cute, his lips so sexy with those catlike eye, gashi dogooo, I guess he have got six packs daga ganinsa yana workout, dama kuma ni bana son namiji fari pau, wllh Mum gayen ya hadu sosai, kuma naga sai wani basarwa yake yana shan kamshi, to ai irinsu nake so" Tun da Imaan taga irin kallon da Mujaheed ke mata bayan sun dau hanya ta kagu su isa gida ta fice daga motarsa tayi ta kanta, gashi dama so take suna komawa gida ta dau Atm card ta tafi supermarket siyo ma Sadeeq abinda ta masa alkawari jiya, a kofar gida Mujaheed yayi parking tana jin ya bude lock din motar ta bude ta fita da sauri, fitowa yayi shi ma bai kai ga bin ta ba tayi tuntunbe bakin gate sai ga ta a kasa, d'agata yyi ta fashe da wani matsanancin kuka tana cewa "Wayyo yaya kafana ya gurde wllh" maidata gun motar yayi fuska daure ya daga kanta yace "Waye kika fita wajensa shekaranjiya da daddare" k'in cewa komai tayi sai kukan da take tana kiran daddy a tsorace, ya wani hade rai cikin tsawa yace "Ba tambayar ki nake ba?" Still taki cewa komai xuciyar ta Sai bugawa yake, murda kunnenta yyi da karfi yace "Are you daft" ta kara rushewa da kuka tace "Don Allah kayi hakuri" yace "Waye shi" cikin kuka tace "Nima ban san shi ba yaya" Ji yake kamar ya sauke mata mari ya dinga mata wani kallo xuciyarsa na tafarfasa, he is just trying hard to control his temper, strictly yace "Toh daga yau Imaan, I mean daga yau.... na sake ganin ki da wani a tsaye wllh sai na kusa sumar dake a gidan nan I promise you that, ba ciwon jiki ko Asthma ba, idan ma jini ke xuba ko ina na jikin ki wllh sai nayi abinda na maki alkawari, ke har guda nawa kike xaki ke tsayawa da namiji jikin mota? How old are you??" Kuka kawai take tana kallonsa duk jikinta na rawa don ta dade bata gansa cikin yanayin nan ba, ya mata tsawa yace "Baxa ki bani amsa ba sai na gaura maki mari?" Cikin rawar murya tace "Ba na kusa 18 ba...." Rankwashi ya kai mata ta dafa wajen tana kiran inna a rikice, yace "In sake ganin ki da wani a waje, sai kin raina kanki wllh" daga haka ya saketa ya rufe motarsa, ta wuce ciki da sauri bata xame ko ina ba sai part din inna, xubewa tayi kan kujera tana rusa kuka, Inna ta fito daki da gudu tace "Na shiga uku me ya same ku a hanya, ko hatsari ku ka yi??" Imaan ta mike xaune cikin kuka tace "Yaya ne ya rankwashe ni kuma ya ja min kunne ni ban masa komai ba innaa" Inna ta xauna kan kujera tayi tagumi a hankali tace "Naga abinda ya isheni bai ishi Allah ba, Wannan yaro dai ya isheni a gidan nan wllh, innalillahi wa inna ilaihi raji'un, A kan wani dalilin kuma ya cuce ki, me kika masa?" Xata yi magana sai ga shi ya shigo, kin cewa komai tayi sai shessheka take hawaye na bin kuncinta, inna tayi mitsi mitsi da ido tace "Mujaheed kana manta cewar akwai hisabi koh, kana mance akwai lahira koh, ni ina jiye maka kada wataran ka karasa gawar da ba taka ba a gidan nan, idan abu ya sami yarinyar nan gaskiya xan rufe ido in mance ni na haifi Ahmadu in maka tijara kotu ta raba mu Mujaheed," Yace "Toh yanxu ma ki tashi a tafi kotun mana, duk ke ke karanta mata tsayawa da samari tun bata kai ko ina ba a titi, idan aure take so ae sai ta sanar da Abbanta ayi mata ba ta dinga tsayuwa da maxaje ba tare da saninsa ba, ita har nawa take, ni nasan wlh Abbanta bai sani ba, halan Ummi bata bata labarin abinda na mata kwanaki ba" Inna ta saki baki tana kallon imaan dake shessheka a hankali, can tace "Amma gaskiya ke munafuka ce Imaan, samm baki da hali, banda munafurci ya xa ayi kiyi sabon saurayi amma kiyi ta nuku nuku kina boye min?? me xai bani da Allah bai ban ba, shi kuma gantalallen bai san kakarki na da rai bane da bai taba cewa xai shigo gaisheni ba? Ko uwar ki ce tace ki boye min ban sani ba" Mujaheed ya dinga kallonta da mamaki, rai bace inna tace "Toh ni dai ba ruwana, dama ana boye abun arxiki irin wannan Ashe, me na maki da xaki boye min sabon saurayin ki Imaan?" Juyawa Mujaheed yyi ya fice daga parlon, Imaan ta kyabe baki tana share idonta tace "Shi fa bai san ko waye ba xai wani dinga ce wa saurayina, ni dai wllh inna ku ce masa ba ruwansa da ni a gidan nan" inna tace "Atoh dama meye hadin ki da shi, kawai ni dai nasan ubansa wan ubanki ne kuma duk ni na haifesu, to bayan wannan bbu abinda ya hada ki da Mujaheed ba dangin iya balle na baba, ke dai kawai ki rabu da shi ya ji da wawancin sa kiyi ta kan ki, banda fitina ma ina ruwansa da lamarin rayuwarki, idan ma saurayin kika yi baki isa ba ne, ko idan kin rasa mijin aure astaghfirullah shi xai aure ki ne?? kar ki sake saurarensa duk saurayi ya kira ki shirya ki fesa turare ki tafi, wa xai xauna biye ta Ahmadu da Bukar ga d'an su ma ya dauko hanya, bokon jaraba kawai ni wllh kina gama sakandari aurar da ke xance ayi mijin yaji da lalurorin ki d'a na ya huta haka shi ma" imaan ta mata wani kallo ta mike tana goge guntun hawayenta ta fice a parlon. Da yammacin ranan daddy ya gama shirin komawa Abuja ya tafi yi ma Inna sallama, ta gama goge gogen da ta ke ta dawo ta xauna tace "Tafiyar na nan yau din kenan" yace "Ehh, jirgi xan bi kada jirgin ya tashi ba ni" inna tace "Toh Allah ya tsare, amma xaka tafi kuma ya xancen da ku ka min kai da Ahmadu jiya?" Daddy yace "Na me fa?" Inna tace "Tafiyar yaran nan su je gaida Hansatu mana" Daddy yace "Ehh Barrister yace xuwa satin da xa a shiga sai su tafi" inna tace "Ehh gwara su je, duk da dai uwarta axxaluma ce amma ina mata fatan Allah ya ji kanta na kuma yafe mata, amma gaskiya shari'ar mu sai a lahira, don ta cutar da ni...." Daddy yace "Haba inna, bayan kuma kin ce kin yafe" a fusace inna tace "Toh ai Allah ba axxalumin bawansa bane, don na yafe ai a duniya nake nufi ba a can ba, kai baka san komai ba wllh, kaga irin abinda uwarta tayi min ne, kishi dama hauka ne, ni dai kawai albarkacin marigayin uban ku yasa nake barin ayi xumunci da 'ya yan da ta mutu ta bari ma, kuma duk yaran ba xuwa gaida ni suke ba" Daddy yace "Ke fa kika ce kin yafe xuwan, kowa ya xauna inda yake" Inna tace "Toh idan bance haka ba ya kake so ince, kai so kake su xo su sa ma kai da d'an uwanka ido, yanxu da ake nisa nisa ba ya fi ba, babu wanda yasan halin da wani ke ciki, sai ku dinga wata magana kai da Ahmadu don ba ku aka cuta ba, yanxu kishiyoyin da bani da hakkinsu ba gashi duk sun mace sun bar 'ya ya duk a gantale ba, to me xa su xo su min bayan ga nawa 'ya yan... Ku uku wllh kun isheni xaman duniya ita ma Hadiza tace ta kusa dawowa kasar nan gaba daya, to me xai dameni, a hada masu goma ta arxiki aje dai a gaishesu, har shi wancan katon Balan dake Abuja su karasa su gaida shi, ba komai Allah ya ba mu lada su kuma aniyarsu ta bi su" Daddy yace "Bari in je inna, Mujaheed xai kawo maki sako anjima" tace "Toh Allah ya tsare, yayi maka albarka, ya kare ka duk inda xaka shiga" yace "Toh Ameen nagode" daga haka ya fita parlon, part dinsa ya tafi suka yi sallama da Ammi yace "Gobe dai Imaan ta tafi islamiyya, xuwa Wednesday nasan xa su yi tafiyar, before than Dr dinta xai kawo mata drugs dinta coz ya dawo" Ammi tace "Toh Allah ya kiyaye hanya ya tsare, ko in taso ta?" Yace "A'a bar ta" daga haka ya nufi kofa ya fita, Yusuf ne ya kai sa airport. Mujaheed ya daga kai yana kallon Abbansa bayan ya gama maganar da yake, a hankali yace "Abba kaga ba a dde da transferring dina nan ba da har xan fara daukan leave gun aiki...." Abba yace "You are just lookin for excuses, na lura gaba daya baka son tafiyar Muhd" ya sunkuyar da kai yace "A'a ba haka bane Abba, kawai naga...." Abba ya dakatar da shi yace "Toh xan ma boss din naka magana" da sauri ya dago yana kallon Abba amma bai ce komai ba, Abba yace "Beside idan ku ka tafi Wednesday xuwa Friday ai kun dawo, nan nan sulejah dai" Mujaheed bai ce komai ba still, jin Abba ma yyi shiru yace "Toh Abba kasan yanayin jikin Imaan, har da ita xa mu je?" Abba yace "Toh ba ga ka ba, you just go with first aid box" Mujaheed yace "Toh shikenan" Abba yace "And ina son dama muyi wata magana Mujaheed" Mujaheed yace "Ina ji Abba" Abba yace "Its high time you think of settling down with a family Muhd, naga baka san shiru ba kai, idan na kyale ka a haka xa ayi ta tafiya, duk abokanka sun yi aure with kids, not even kid, to kai me kake jira son?" Ya shafa kai a hankali yace "Abba warce nake nema tana karatu ne, amma ta kusa karewa nan da 'yan watanni in sha Allah" Abba yace "Yar ina ce?" Ya d'an yi murmushi yace "Nan Kaduna, a hayi iyayenta suke amma tana gun yayarta a Unguwar sanusi" Abba yace "Toh maa sha Allah, hakan yayi kyau sosai, but I think it's better a fara magana tun yanxu...." Muryar Umma suka ji tace "Babu maganar da xa a fara Alhaji" duk suka daga kai suna kallonta ta karaso cikin parlon, bacin rai karara fuskarta tace "Yanxu ni xaka munafurta Mujaheed, haka muka yi da kai, to kasani wllh idan ina numfashi a doron kasa baxa ka auri yarinyar nan bar, idan kuma kana son ganin ba dai dai ba a lamarin ka kaci gaba da alaka da matsiyaciyar yarinyar, ina zamana ka dauko mun talauci a matsayin surka, to wllh kayi kadan gwara kayi ta xama ba auren ya fi, ga yarinya mai hankali mai natsuwa Safeenah yar wajen Hajiyan Marafa can na nema maka yarinyar kuma tayi mugun na'am da kai xaka toxarta ni ka maidani karamar mutum a idonsu???" Abba yace "Abinda nake son in fara fahimta a nan shine, la6e kike min Rukayya?" Umma ta tabe baki tace "Idan ma la6en nayi Allah ne yasan bani da hakkin kowa shi sa har ya bani ikon labewan in ji komai, Alhaji wato idan Kasan talauci to a kan yarinyar da iyayenta ya kare, can wani ghetto fa suke, to idan ba toxarta mu Mujaheed ke son yi a idon jama'a ba ina shi ina yarinyar nan, Kyan banxa kyan hofi, yo ina ma take da kyan ita ba wai fara ba, gaskiya kayi min iyaka da Mujaheed kada in nuna masa 6acin raina a gidan nan, sam baxai ji da dadi ba, shi baya koyi da d'an uwansa Yusuf, dubi fa yarinyar da yake nema yar attajiri gashi har magana yayi nisa, sai ni ce Mujaheed xai cuta ya kwaso min yar talakawa" Abba ya girgixa kai yace "Halan ke ke raba talauci da arxikin Rukayya?" Umma tace "Ba ruwana da wannan xancen ni dai gaskiya idan Mujaheed bai yi hankali da ni ba xai sha mamaki, kuma in dai baxai bi ni sau da kafa ba xai dinga ganin ba dai dai ba a lamarin sa ni dai ba ruwana" tana kai wa nan ta fice fuuu, Abba ya girgixa kai yace "Look son, ba ruwanka da wannan uwar taka, ba isasshen hankali gareta ba am giving u my words, ka ci gaba da neman yarinyar, Allah ya shige mana gaba" A hankali Mujaheed yace "Ameen" Abba yace "You can go" ya mike yace "Nagode Abba" daga haka ya fita parlon. A hankali Ammi ta bude kofar dakin Imaan tana kallon ciki jin dariyar da take cikin duvet, da sauri Imaan ta katse wayar ta tura karkashin pillow jin kamar an bude kofa, Ammi ta kunna wutan dakin tace "Da wa kike waya Imaan?" Bude duvet din tayi kamar mai bacci ta mike xaune tace "Na'am" Ammi ta mata wani kallo tace "Baxa ki amsa min tambayata ba, da wa kike waya nace?" Shiru tayi tana kallon Ammi kamar xata yi kuka, Ammi ta karasa kusa da gadon tace "Bani wayar" ba musu ta ciro wayar ta mika ma Ammi, Ammi na kallon call log tace "Number waye wannan din" murya can kasa Imaan tace "Abokin ya Muhsin ne" Ammi tace "Me ya hada ki da abokin Muhsin, a ina kika san sa?" Tace "Ammi yana xuwa gidan gwaggwo kuma kanwarsa classmate dita ce, yanxu ma kawai tambaya ya kira ni yake min ba wani abu ba" Ammi ta dinga mata wani kallo, ta sunkuyar da kai, Ammi tace "Ke dai kin iya munafurci" kamar xata yi kuka tace "Ammi ni wllh dai ya kira ni ne amma ba komai fa" Ammi tace "Toh yayi kyau, ki bude kunne sosai ki saurareni, kada ma ki nuna nasan kina waya da wani a gidan nan don ba ruwana, duk ranan da Daddyn ki ya kama ki dama ki tanadi abun gaya masa don't involve me in this" tana kai wa nan ta fice dakin. Washegari da rana Ammi na xaune parlor Imaan ta fito sanye da Hijab sai karamar jakarta da ta rataye, Ammi na kallonta tace "Ina xa ki?" A hankali tace "Ammi xan je in siyo cream a supermarket" Ammi na kallonta da mamaki tace "Yaushe na siyo maki da har ya kare Imaan?" Shiru tayi tana kallon Ammi kamar munafuka, Ammi tace "Shan cream din kika fara?" Tace "Ammi shafawa kawai nake yi fa" Ammi ta tabe baki tace "Toh ni kam bani da kudin cream yanxu" tace "Ai ina da kudi a account dina" Ammi tace "Toh Hajiya mai kudi, a dawo lafiya" yar dariya tayi ta sa flat shoe dinta ta fita parlon, kamar mai tausayin kasa ta taka har bakin main road inda xata samu adai daita, jin wayarta na vibrate a jaka ta fiddo, Sadeeq ta ga ke kiranta, ta daga ta kai kunne, Cikin cool voice dinsa yace "How r you Imaan?" A hankali tace "am fine ina yini?" Yace "Lafiya lau, kina hanya ne?" Tace "Ehh" yace "Ina xa ki?" Ta d'an yi shiru kafin tace "Xanje supermarket" yace "Wanda muka hadu ranan?" Tace "Ehh" yace "Tell me what you want to get sai in siyo in kawo maki yanxu" da sauri tace "A'a bana so" a hankali yace "Why?" Tace "Ni dai bana so, yanxu ma xan hau adai daita ai" yace "Toh shikenan, we will talk later, Allah ya tsare" tace "Ameen thanks" daga haka ya katse wayar ta samu adai daita ya kai ta har mall din, wani babban boutique dake opposite mall din ta shiga, gun eyeglasses ta tsaya tana duba glasses masu kyau shigen irin wanda yake sa wa, ta wara ido ganin the prices are waoww, wani da ya mata kyau sosai ta dauka tana dubawa kafin ta tafi gun da ake biyan kudin kayan ta basu atm suka cire kudinsu suka mata packaging din eye glass din ta fita ta tsallaka ta shiga cikin mall din, gun body creams ta tafi ta dau cream da take shafawa duk da akwai mai yawa a gida, kawai dai ta juye a wani container ta boye ne sanin Ammi na iya shiga daki ta duba bayan ta taho, bayan ta dau cream din xata juya ta kusa cin karo da mutum, komawa baya tayi da sauri da nufin basa hakuri, sai kuma ta xaro ido da mugun mamaki tana kallonsa, murmushin da ya bayyana dimples dinsa yyi yace "Sorry" ta sunkuyar da kanta yace "Har kin gama shopping din ko yanxu kika fara" ta dauke kai tace "Na gama" yace "Toh mu je ki rakani I want to get somethings" Daga haka ya fara tafiya, bin bayansa tayi kamar munafuka, gun kayan ciye ciye su chocolates, biscuits sweets da dai sauransu ya tafi, yana kallonta yace "Kanwata xata yi birthday gobe, so nasan dai ku mata babu abinda ku ke so da ya wuce wannan, am asking for a favor duk abinda kika san kina so ki daukar mata nasan ita ma xata so" Murmushi tayi tace "Ohk then" nan ta dinga jidan duk abinda ya kwanta mata take mugun so kuma, ya dinga tura trolley din yana biye da ita, xaro ido yyi yace "Anya imaan wannan banda mugunta kuwa, yanxu duk wannan abubuwan da kike dauka kina nufin kina son su?" Ta juya ta wara masa manyan idonta tace "Ai duk abinda kaga na dauka a nan I love it with all my heart, baka san yanda nake son chocolates da sweets ba koh" murmushi yyi yace "Toh mu bar mata su a haka" tace "A'a jira ga wani chocolate can..." Da sauri ta tafi ta debo har biyar ta xuba a trolley, ta kwaso wasu biscuits ma ta xuba, ta dau wani sweet ta xuba shi ma, ta juya tana kallonsa tana murmushi tace "Toh ni dai ina mugun son teddy in daukar mata" ya langwabar da kai yace "Kawai so kike account dina yayi kuka yau koh??" Ta hade rai tace "Just guda biyu ko uku fa, Is she not ur sister? And is it not her birthday" daga haka ta tafi gun teddies ta debo uku masu tsada da kyau ta jefa cikin trolley din tace "Tunda kana complaining account dinka, mu bar mata su a haka kawai" Yar dariya yyi yace "Noo ci gaba har sai kin gaji" tace "A'a I have conscience" dariya yyi ya bi bayanta ganin ta nufi gun counter, cream dinta ta ajiye xata bada ATM card ya riga ta mika nasa, juyawa tayi tana kallonsa sosai gabanta ya fadi bayan sun hada ido tayi saurin sunkuyar da kanta, nan aka cire kudin aka bata receipt dinta, ta taya sa ciro abubuwan cikin trolley din shima ya bada atm card aka cire aka masu packaging, barinsa tayi da kayan gaba daya ta dau teddies din suka fita. Bayan ya xuba ledojin a bayan mota ya rufe motar yana kallonta kafin yace komai tace "Yau ne birthday din?" Gyada mata kai yyi smiling, ta boye fuskarta a hankali tace "Toh ni dai ina son kaza ko xaka siya mata" Wara ido yyi yana kallonta, sai kuma yyi dariya yace "Ina kika ga kaxa imaan?" Ta turo baki ta nuna masa inda ake gashin kaji, yana murmushi ya tafi, ya siyo kajin gasassu biyu ya dawo ya sa a mota, ya juya yana kallonta pleadingly yace "Let me drop you plss" da sauri tace "Nooo thank you" tana fadin haka ta bude karamar jakarta ta fiddo glass din dake leda tana kallonsa ta mika masa, a hankali ya sa hannu ya amsa yana kallon kwayar idonta, hakan yasa tayi saurin sauke nata idon, bude ledan yyi ganin glass din underneath his breathe yace "Waow..." Murmushi tayi xata juya masa baya ya riko hannunta cikin sanyin murya yace "Thanks Imaan, I love it..." Bata ankara ba sai gani tayi yyi pecking hannunta, ta kwace hannun da sauri tana xaro ido a tsorace, shi ma daburcewa yyi yace "I... Sorry I.. I am just happy imaan, I love the glasses" ta kirkiri murmushi har sannan tana jin warm lips dinsa a hannunta, xata juya yace "Wait Imaan" tsayawa tayi gabanta na faduwa, ya bude front seat yace "Plss let me drop you home" kasa ci gaba da kallonsa tayi ta kuma kasa cewa A'a, a hankali ta shiga motar yyi murmushi ya rufe, ya xaga ya shiga driver seat suka bar mall din, bata yrda yaje dai dai gate din su ba tasa ya ajiye ta few houses away from theirs, ta bude motar ta sauka shi ma ya sauka ya xaga ya bude back seat, ya fiddo gaba daya ledojin siyayyar da suka yi da teddies da kajin duk ya ajiye kusa da ita ya wara ido yana mata murmushi yace "Dama duk naki ne" bai jira cewarta ba ya xaga ya shiga driver seat ya tada motar ya bar ta da zare ido ya bar layin, kallon ledojin ta dinga yi kamar xata yi kuka, yanxu ya xata yi da kayan nan.... Kwasa tayi ta boyesu cikin flowers ta dinga dauka da daddaya da daddaya tana kai su part din inna, duk a mugun tsorace take, Inna ta saki baki tana kallon kayan, imaan ta tafi dauko last ledan, Yusuf dake ta kallonta tun shigowarta na farko ya mike ya isa kusa da ita da mamaki yace "Daga ina kike wannan saurin hakan Imaan, what's all this u are taking in" kin tsayawa tayi tana kirkiran murmushi ta wuce sa da sauri, tsoronta daya kar ta gamu da Mujaheed, har dai ta isa parlon inna, Inna dake tsaye bakin kofa har lkcn ta sake baki tana kallon uban ledojin ta bi ta da kallo har ta ajiye na hannunta, Inna tayi kasa da murya tace "Imaan ina kika samo wannan kuma?" Imaan ta kwashesu gaba daya ta kai dakinta da sauri duk ta ajiyesu sanin Yusuf xai iya biyota, Tana fitowa dakin tace "Ni dai kawai kiyi shiru inna kar ya Mujaheed ya sani wllh duka xai min" Inna ta hade rai tace "Duka?? da kuwa ya dokar ma kansa fitina da bala'i, kuma da karshen xamansa ya kama a gidan nan" Imaan ta xauna saman kujera har sannan gabanta bai daina faduwa ba, Yusuf ne ya shigo parlon, inna ta wani tsuke fuska, yana kallon Imaan yace "Daga inna kike Imaan?" Inna tace "Yau naga jaraba, to ina ruwanka isuhu ko ka aiketa ne? Ku dai 'ya yan Ahmadu ku daina sa ido wllh, meye kuma wani daga ina take kamar xamanka take a gidan, ni dai ba ruwana, ku dinga tsoron Allah kuyi mai fishshe ku a gidan nan" juyawa Yusuf yyi ya fita parlon, inna ta kulle kofarta ta sa makulli, ta kalli imaan tana murmushi tace "Kar dai sabon saurayin ne yyi maki uban siyayyar nan takwara" Imaan tace "Wllh kar ki gaya ma kowa idan ba haka ba kazar ma baxan tsam maki ba" Inna tace "Ke ma dai da wata magana wllh, sai kace wata yarinya?? Wa xan gaya ma ni patuu, wannan ai sirri ne tsakaninmu" Imaan ta shiga ta fiddo ledan kajin guda biyu tace "Toh idan yaya ya shigo fa?" Inna tace "Oh oh Allah, waye kuma wani yaya, ina ruwana da shi, ko me xai xo ya min? Ko ya xo ma ni baxan bude kofata ba bbu ruwana, idan ma ya xo damuna yake ba abinda yake tsinana min" *The book Imaan is not free, you read for free ur cup of coffee*🤷🏻‍♀️ It's 300 via Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah Then u show ur evidence of payment via my WhatsApp digit 07087865788 to be included in the payment group.Ammi ta bi Imaan da kallo ganin xata shiga daki tace "Kee" juyowa tayi tana kallon uwarta ta, Ammi tace "Ajiye min plate din kika yi kika fito?" Imaan tace "Ammi na wanke wllh" Ammi tace "Toh ki tafi ki sha maganinki ki daina min wannan yatsine yatsinen da kike yi" a hankali tace "Na sha Ammi, kai na ke min ciwo da bayana" Ammi tace "Allah ya sauwake" Har Imaan zata shiga daki sai kuma ta fasa ta dawo ta xauna kusa da Ammi murya can kasa tace "Ammi don Allah idan na gaya maki abu baxa ki min fada ba?" Ammi na kallonta tace "Idan ya kama in maki fada ae dole in maki" Shiru tayi tana kallon Ammi, Ammi tace "Ina jin ki" Sauke idonta kasa ta yi tace "Dama..." Sai kuma tayi shiru, Ammi tace "Dama me?" Murya can kasa tace "Wannan mutumin da kika ji ina waya da shi da daddare shine da naje shopping mall daxu muka hadu" Marairaicewa tayi tace "Ammi wllh ban san ma ni ya siya ma ba" Ammi tace "Me ya siya maki?" Ta ja baya kadan tace "Chocolates, da abubuwan ci...." Ammi ta dinga kallonta, kafin tace "Ina suke?" Imaan na kara matsawa daga kusa da ita tace "Na kai part din inna, ina tsoron kar ki min fada" Ammi tace "Ni xa ki ma karya baki san xai siya maki ba koh??" Kamar xata yi kuka tace "Wllh Ammi ban sani ba, we just met at the supermarket" Ammi tace "Toh shi yaron a ina kika san sa?" Tace "Ai na ce maki abokin ya Muhsin ne kuma Yayan Classmate dita Mariya ce, a gidan gwaggwo muka hadu" Ammi tace "Toh yyi kyau, you had better be careful Imaan, kin san Abbanki won't take it likely with you if he should find out, ni dai kar ki ja min matsala bbu ruwana, banda shashanci ya maki yawa you ought to have known ur left from right now" shiru Imaan tayi bata ce komai ba, can ta mike a hankali ta wuce dakinta. Mujaheed na zaune parlon inna bayan ya dawo aiki ran Tuesday ita ko tana can tana shara, Imaan na kwance tana bacci kan 3 seater, tun da ya kalleta sau daya bai sake kallonta ba, bayan wani lkci inna ta shigo parlon, kakkabe kujeru ta dinga yi tana cewa "Ni dai gaskiya wannan yarinya ta Bukar tana takurani duk ta kare min kujerun sun lotse, sai dai naji kunya idan nayi manyan baki, yarinya dai kamar kyanwa kwanciya baya karewa, gashi yau laluran ciwon kafar ya tashi bata je islamiyyan ba ma, Allah ka dubi jikata ka yaye mata wannan bala'in da ba a san kansa ba, ni bari ma kwanan nan xan shirya inje in samu ta Rasulu in ji yanda xa ayi, sai dai duk abinda Ahmadu da Bukar xa su ce su ce, ai dai ba gun boka xa mu je ba" ganin ruwan kumfa inna ke kokarin kadawa Mujaheed yace "Ni dai magana na xo mu yi, ki bar wannan aikin naki da baya karewa ki saurareni" ta kallesa ce "Toh idan aiki ya kare ae kazanta ta tabbata kenan, ni ko ina xan yarda in daina aiki in mutu cikin dauda, ko kai baka ji dadi da kamshi da ka shigo parlon ba" yace "Abba nake son ki yi ma magana inna, wllh bana son tafiyar nan, ruwan garin ma ba iya sha nake ba balle abinci, kwanaki da muka je da ku har muka dawo ni ban ci abun kirki ba fa" Inna ta saki baki tana kallonsa, can tace "Toh yanxu ya kake son ayi?" Tace "Kawai ce ma Abba za ki yi xa ki aikeni kano in kai maki wani sako sai Yusuf ya kai su gaskiya" inna tace "Tohhh, yanxu kiransa xan yi kenan?" Yace "Ehh ki kirasa, sae kice masa ya min magana don kinsan in kece kika min ba xuwa maki aiken xan yi ba" Inna ta mike ta dauko wayarta tace "Toh kirasa" Dialing number Abba yyi ya sa a speak on ya mika mata, imaan sai tsaki take tana turo baki ita a dole an hanata bacci, sai dai ba wanda ya tanka ta, Abba na d'aga kiran inna tace "Yaro??" Abba yace "Ina yini" Tace "Toh lafiya lau, sae dai wuni nayi ina aiki wllh har bayan window na duk na share, na goge gilashin windon" Yace "Alhmdllh, fatan dai lafiya?" Ta gyara xama tace "Ina fa lafiya, wato kai dai ka haifa ma kanka fitina da abinda ya fi karfin ka ne baka sani ba har yanxu Ahmadu, wai dama don Allah ina ne asalin ko wani mutum dai bahaushe?" Abba yace "Ban gane ba inna" a d'an fusace tace "oh oh Allah, Asalin kowa nake tambayarka, ina ne asalina da na Ubanka?" yace "Asalin kowa kauye inna" Inna tace "Toh Alhmdllh, yanxu wannan mutumi Mujaheed ya xo ya sameni, ko gaisuwar kirki ba mu yi ba, ya fara bani sako in baka, wato cewa yyi ince maka shi baxai je kauye ba gaskiya, don kwanaki ma da mu ka je a gantale ya dawo ba abinci, har yana koya min karyar da xan maka na cewa xan aikesa kano ko uban wa gareni kano oho, wai sai Yusuf ya kai su kauyen, bai san ni yar gaskiya bace, ba a cin amana da ni, yanxu fisabillahi Ahmadu in ji kaga abinda yasa tun suna yara nake cewa ka dinga kai su can koh?" Mikewa Mujahedin da ya bude baki yyi yana kallonta, imaan ta sauko kasa ta dinga 6a66aka dariya, Abba yace "Toh yayi kyau ki kyalesa kawai, sae su tafi da Yusuf din" inna tace "Atoh, ni dai ba ruwana, ka tashi tsaye da rokan Allah kan Mujaheed" daga haka ta katse wayar ta tayi kasa da murya tana kallon Mujaheed tace "In dai ranka bai kwanta xuwa kauyen ba kada kaje gaskiya, duk bambamin da Ahmadu xai yi xuba masa na mujiya, haka kawai kaje ka cutu, don gaskiya ko ni bana cin abincin gidan hansai, to idan na ci na tsuge da xawo ya za ayi da ni???" Mujaheed ya juya a mugun fusace xai fita jin dariyar da Imaan take ya juyo ya haureta da karfi ya fice, wani ihu ta fasa ta rike kafar, inna ta mike da sauri tace "Fita ki bisa ni ba ruwana kada a dameni ya xa mu dinga magana ki mayar da mu mahaukata kina dariya" Imaan ta mike tana kuka sosai ta fita parlon tana dingishi ta wuce part din su, Ammi ta fito kitchen da sauri, Tace "Lafiya, me ya faru?" Cikin kuka tace "Yaya ne ya haure min kafar dake min ciwo da karfi gashi yanxu ya rike Ammi, Wllh ban masa komai ba" tana fadin haka ta xube kan kujera tana kuka sosai, Ammi ta karaso tana kallon kafar, har gun ya tashi yyi ja, Hijab dinta ta dauka ta sa ta fita parlon bata xame ko ina ba sai bangarensu, Yana xaune dinning takaici ya ishesa Anty kuma na kitchen da su Maimoon. Nan parlon Ammi ta tsaya tace "Mujaheed me Imaan tayi maka ka haureta a kafa?" Kallonta yyi ya dauke kai bai ce komai ba, ta karasa dinning din fuska daure tace "Tambayar ka nake malam, ka fara hauka ne xaka haureta a kafa, to Wllh even by mistake kada ka sake don zan dau mummunan mataki a kanka" Anty ta fito kitchen da sauri tace "Lafiya Hajiya Aisha?" A fusace Ammi tace "Wllh ku ja masa kunne ya fita harkar Imaan a gidan nan, duk ranan da ya sake gangancin ta6a lafiyarta xa ayi tashin hankali a gidan nan, haka kwanaki ya mareta na kai xuciya nesa ban ce komai ba, to this shud be the last, kada ya sake idan ba haka ba wllh sai na rama mata" Hakuri Anty ta dinga bata, Mujaheed ya mike ya wuce sama ba tare da ya sake kallonta ba, Ammi ta nufi kofa xata fita suka kusa cin karo da Umma xata shigo sun dawo anguwa da Rahma, ko kallonsu bata yi ba ta fice, tana komawa dama daki ta shiga ta dauko man xafi ta fito ta shiga shafa mata a gun, Imaan ta dinga yarfe hannu tana kiran daddy, bayan Ammi ta daina shafa wa a hankali tace "Ammi xuwa kika yi gun yaya?" Ammi tace "Baxan je ba ko shi ya haifa min ke?" Imaan na kallonta tace "Fada kika masa" Ammi tace "Abinda ya fi fada ma" imaan ta zaro ido tana kallonta, can tace "Ni da baki je ba Ammi ni ne fa nake ta masa dariya...." Da gudu ta mike bayan ta kauce marin da Ammi tayi niyyar sauke mata, ta wuce daki tana turo baki ta kulle kofar ta sa key, tana jin Ammi na cewa "Xaki fada min ko kanin ubanki ne yayan, daga yau ma kika sake xaunawa inda yake wllh sai na kakkarya ki a gidan nan" Inna ta saki baki tana kallon Mujaheed har ya gama, tura tuwon gabanta tayi tace "Ba lafiya, ita Aishar? To yaushe ta xama haka, atoh gaskiya imaan dai ta zama yar jaraba tunda akan ta uwarta taje tana maka bala'i, wato Allah kadai yasan abinda yarinyar ta tsara ma uwar, saboda irin wannan halayyar tata yasa aka rasa gane kan ciwonta fa har yau, to meye kuma yarinya karama da hada gurmi a gida, ae da sai kace ma Aishar A'a ni ba ruwana baxan yi fada da ke ba don kin haifeni, ai ke kusan sa'ar uwata ce, to kawai kuma sai ka tsaya kallonta kayi shiru" Mujaheed yace "Ni baxan ce mata komai ba ko sbda daddy, amma ta sake min haka a gidan nan gaskiya sae dai duk abinda xae faru ya faru" Inna tace "Ni ko sai naje na sameta wllh" da sauri Mujaheed yace "A'a kar ki ce mata komai" Inna ta ja tsaki tace "Ba dole in sameta ba xata sa ka gaba tana jaraba a kan figaggiyar yarinya mai hada gurmi" tana fadin haka ta fice parlon, Ammi na shafa ma Imaan man xafinta a kafa Inna ta shigo ba ko sallama, Ammi ta mike tace "Sannu da xuwa inna" inna tace "Aa ba wani sannu da xuwa, yanxu Aisha a kan yar ki xa ki sa Mujaheed gaba kina masifa inda kike shiga ba nan kike fita ba kamar xa ki make sa, to ma ina ruwanki kina 6are xa ki shiga harkan 'yan uwa, ubansa fa wan ubanta ne uwa daya uba daya, to ke kuma a wa Allah na tuba, Ba kunya ba tsoron Allah xaki shiga fadan 'yan uwa, abinda ma ina xaune parlon d'an shafa kafar nata yyi ya fita shine munafukar nan ta dinga ihu tana min birgima ni kuma na koreta, ni dai ba ruwana kar ki lalata mana xumunci gaskiya, ko xane Imaan Mujaheed yyi yau kanwarsa ce kuma yana da ikon yin haka, to banda shi da ya tsaya mata kan lalurorinta shekarun baya da ba sai dai ta mutu ba, ni dai a dinga jin tsoron Allah, gashi nan dai albarkacin Bukar bai kula ki ba, toh ni dai kada a sake sa min jika a baki ba ruwana, banda ma bifillatani agwai da wauta ina shi ina shiga sha'anin family" tana kai wa nan ta fice a parlon, Ammi ta rufe man hannunta tana kallon Imaan tace "Wllh na sake ganin ki xaune inda Mujaheed yake a gidan nan sai na kusa sumar da ke" Imaan dai ba ta ce komai ba. Misalin sha daya Imaan ta mike daga kwancen da take da kyar xata shiga daki ta kwanta, duk jikinta ciwo yake mata ga wani xafi da jikin yayi, Ammi dake xaune parlon tace "Kina ji na" imaan ta juyo tana kallonta, Ammi tace "Dama gobe kice masu baki jin dadi baxa ki iya tafiyar ba, don babu inda xa a dake, ina xaman xamana a kwaso min wahala a bar ni da jiyya" Imaan tayi shiru tana kallonta, can tace "Toh" daga haka ta wuce cikin daki ta kwanta. Washegari karfe tara su Maimoon, Ummi da Rahma suka gama shirin su na tafiya, kaya kala biyu ko wannensu ya dauka Abba duk ya basu kudin kashewa, Yana kallon Ummi yace "Tafi ki duba ko mamana ta gama shirya wa" Ummi ta fita parlon xuwa part din su Imaan, Ammi ta fito daga bedroom din Imaan kenan rike da cup din shayi don da mugun xaxxabi ta tashi safiyar ranan, Ummi ta shigo parlon da sallama, gaisheta tayi tace "Abba yace Imaan ta fito" Ammi tace "Ae kam yau ta tashi babu lafiya" Ummi na komawa ta fada ma Abba haka, Abba yace "Subhanallah ba lafiya kuma" mikewa yayi ya fita, a dai dai part din su Imaan ya hadu da Mujaheed ya dawo daga bangaren inna, Abba yace "Imaan wai bata da lafiya yau" Mujaheed yace "Subhanallah" Abba yace "Let me check on her" Mujaheed bai ce komai ba kamar ya juya yayi tafiyarsa sai kuma dai ya bi bayan Abba, Ammi suka gaisa da Abba, Mujaheed yayi kasa da kai ya gaisheta, Ita ma ba tare da ta kallesa ba ta amsa bbu yabo bbu fallasa, Abba yace "Toh ya jikin nata?" Ammi tace "Toh da sauki, tun jiya dama bata jin dadi" Abba yace "Ikon Allah" Ammi tace "Tana ciki" Abba ya nufi dakin nata, Mujaheed ya bi bayansa kansa a kasa, kwance suka sameta cikin duvet amma still sai shivering take, Abba ya cire duvet din yace "Sannu mamana" Bude idanuwanta da suka rina tayi a hankali, Abba yace "Ina ke maki ciwo" girgixa masa kai kawai tayi, Mujaheed ya duka kusa da ita a hankali ya kai hannunsa jikinta, Abba na kallonsa yace "Ko dai a tafi asibiti" Mujaheed xai yi magana aka bude kofar dakin inna ta shigo a rikice tace "Ahaf, ni dama nasan xa a rina, ba ayi hauri ba ma ya aka kare balle anyi, wllh Ahmadu da ya tattakure ya tattakure kawai sai gani nayi ya haureta" *The book Imaan is not free, you read for free ur cup of coffee*🤷🏻‍♀️ It's 300 via Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah Then u show ur evidence of payment via my WhatsApp digit 07087865788 to be included in the payment group.Abba ya juya ya kalli Mujaheed jin abinda inna tace, Imaan ta mike xaune da kyar tace "Ba fa kafana ke ciwo ba" Inna tace "Toh ina ke maki ciwo" Komawa tayi ta kwanta bata tanka ta ba, Ammi dake tsaye bakin kofar dakin sai kallonta take, Abba na kallon Mujaheed da ya kasa cewa komai yace "Amma me yasa xaka haureta jiya?" Ya sunkuyar da kai yace "It wasn't intentional" Abba ya gyada kai yace "It wasn't intentional, OK that's good kayi kokari" Daga haka ya juya ya kalli Ammi yace "Ta shirya ta fito mu je asibiti" daga haka ya fita dakin, Mujaheed ya harari Inna fuska daure xai fita tace "Oho dai ta rufa ma ka asiri amma ko tantama babu haurin da ka mata ne ya ja mata wannan ciwo" Ammi ta basa hanya fuska daure, kansa a kasa ya fita dakin, Inna tace "Kyansa duk inda imaan xata ga Mujaheed daga yanxu ta gudu tayi ta kanta, ni dama tun da naga yanda yake laftar 'ya yan jama'ah a anguwa yana d'an yaye bai fi shekara 3 ba nasan akwai bala'i a gaba wllh, duk ya bi ya addabi 'ya yan mutane da cizo da yakushi a anguwa, kowa ya gansa sai ya adana d'an sa, lkcn d'an Hansai Garba na kamarsa kullum sai ya ciji garba yakushesa, Hansai tayi ta jin haushi don ta xo jegon Huraira a gida, in takaice maki kafin Hansai ta bar gidan idan aka bude jikin garba duk ta6on cixon Mujaheed ne, to kuma meye baxai yi ba yanxu?" Imaan na daga kwance sai dariya take da kyar, Ammi dai ko kallon Inna bata yi ba tana fiddo ma imaan kayan da xata sa, inna tace "Toh Allah dai ya kiyaye gaba yyi maki tsari da shi, amma gaskiya imaan ki guji duk inda Mujaheed yake, idan kun dawo asibitin xan xo dubaki idan Allah ya yarda, tafiya dai ta sha ruwa" daga haka ta fita dakin, Ammi tace "Kin tashi kin shirya ko xaki kwanta nan kina dariyar walakanci ne?" Imaan ta tashi ta saka kayan da Ammi ta fiddo mata, Inna na fita taga Abba tsaye a waje, tace "Ahmadu tafiya dai ta sha ruwa koh?" Yace "A'a xa su wuce tare da Yusuf yanxu, shi Mujaheed xa su je asibiti da Imaan" inna tace "Toh madallah, hakan ma yayi, to ko in bisu asibitin ne" Ta gefen ido Mujaheed ya kalleta da sauri, Abba yace "Ehh to xa ki iya bin su" Tace "Toh bari in kulle dakina kada a barsa a bude gaskiya" daga haka ta wuce sashin ta, Mujaheed ya nufi motarsa don fitar da motar waje, Abba ya bi sa da kallo har ya isa parking space ya shiga motar, Imaan ta fito sanye da Hijab har kasa, da kyar take tafiyar, Abba yace "Sannu mamana, Allah ya sauwake" a hankali yace "Ameen" yace "Mu je can kofar gidan, ban gane fita da motar da yayi ba" tare suka fita compound din, Ya bude ma Imaan front seat ta shiga, Abba na kallonsa yace "Inna na tahowa yanxu, tare xa ku tafi" yace "Ehh na sani" Daga haka Abba ya koma cikin gida, Mujaheed na ta kallon gate har sai da yaga inna ta fito tana washe baki sannan ya ja motarsa yayi zooming off, Imaan ta xaro ido tana kallonsa, yana isa titi ya kashe wayarsa ya ajiye ya dau hanyar asibitin da yake aiki, Sai da suka yi nisa fuska daure yace "Ni kika je kika hada da mamarki koh?" Tace "Ko dai ita taga ina kuka" ya gyada kai yace "Xa ki gane kuran ki" Ta turo baki ta jinginar da kanta da kujera, Suna isa asibitin bayan yayi parking ya juya yana kallonta yace "Sauko min a mota" Bude ido tayi da sauri, ya bude door din motar ya fita, a hankali ta ta bude side dinta ta saukar da kafafuwanta kasa, xagayowa yyi ganin bata fito ba yace "Baxa ki sauka ba" kamar xata yi kuka tace "Wllh jiri nake ji yaya" Wani harara ya watsa mata yace "To daukan ki xan yi?" Bata ce komai ba ta sauko motar, ya rufe ya kama hannunta suka shiga cikin asibitin. Yana xaune office misalin sha daya bayan ya kunna wayarsa kiran Abba ya shigo wayar, murmushi yyi ya daga ya kai kunne, Abba yace "What's taking you people too long Mujaheed" yace "Drip aka sa mata Abba, jikin da sauki sosai, she is fast asleep now" Abba yace "Toh Allah ya sauwake, why did u left inna behind?" Yace "Abba Kasan yanda take abinta, xuwa xata yi tayi ta fada every slight mistake" Abba yace "Haka ne, da yaushe xa ku dawo kenan" yace "Nan da azahar in sha Allah" yace "Toh Allah ya kai mu" Mujaheed yace "Ameen" daga haka Abba ya katse wayar, Mujaheed ya juya yana kallon Imaan dake kwance kan gadon duba pregnant women tana bacci, mikewa yyi ya isa kusa da ita yana kallon ruwan da ya kusa rabi, Hannu ya kai forehead dinta yaji da dumi har sannan, ta bude ido a hankali, daure fuska yyi yace "How are you feeling now?" Yamutse fuska tayi tana son mikewa xaune yace "Lie still and answer my question" murya can kasa tace "Kai na yana min ciwo" yace "Shi kadai?" Tace "And am hungry" ya kalli abincin da ta ki ci da yawa daxu kafin a mata alluran a sa mata drip ya dauka ya bude ya ajiye kusa da ita ya daga ta xaune, xaro ido tayi tace "Yaya abincin daxu kuma??" yace "Kin taho da abinci daga gida ne" ta hade rai tace "Ni dai baxan iya ci ba bayan ya huce kuma an ajiye k'ura ya gama shiga ciki" wani kallo ya mata yace "Toh sai ki tsaya da yunwar ki ai, wannan abincin dake rufe meye ya samesa da baxa ki ci ba, Bayan har ynxu ma da dumi abincin" yana fadin haka ya dau cokalin ya debi abincin ya kai baki, ta tabe baki ta dauke kai tace "A'a ni dai bana so, tun da safe fa, ko ta gefe gefe ai dust xai iya bi ya shiga, sai dai kai ka cinye a kawo min wani" Yace "Toh xaki ga wani kuwa" daga haka ya kai abincin table dinsa ya xauna ya fara ci, ta dinga kallonsa kamar xata fashe da kuka, ganin ko kallonta bai yi ba tace "Ni dai ka bani waya in kira Ammina ta kawo min abinci" yace "Baxan bayar ba" komawa tayi ta kwanta ta fara kuka har bacci ya sake xuwa mata, mikewa yyi ya rufe sauran abincin da bai cinye ba ya fita office din. Wani takeaway din ya fita ya siyo mata na abinci, yana dawowa ya tasheta ya ajiye mata abincin a gabanta sannan ya juya ya fita, ta mike xaune ta bude abincin ta fara ci a hankali, har ya dawo dakin bata gama cin abincin ba, ya xauna kan office chair dinsa, tana kallonsa tace "Yaya ni baxan iya cinyewa ba" bai tanka ta ba hankalinsa na kan laptop din gabansa, ya gama abinda yake sannan ya juya yana kallonta ya ga ta ajiye abincin ta kwanta, mikewa yyi ya karasa kusa da ita ya dauke abincin ya ajiye ta bude ido tana kallonsa tace "Yaya ina son xan yi magana da Ammina" yace "Baxa kiyi ba" yana fadin haka ya koma table dinsa, ta turo baki ta juya masa baya. Karfe biyu Imaan ta bude ido jin an kama hannunta, ya karasa cire mata drip din yace "How are you feeling?" Ta mike xaune da kyar tace "Da sauki, I want to go home" Yyi disposing roban ruwan ta sakko saman gadon, da sauri ya rikota ganin xata fadi duk da ita ma ta kama gadon, kamar xata yi kuka tace "Wllh jiri nake ji yaya" Ya saketa yace "Toh ni nace ki sakko?" Komawa saman gadon tayi ya fita dakin, ba a dau lkci ba ya dawo ya dau wayarsa da car key yace "Mu je" ta xaro ido tace "Idan na fadi fa?" Yace "Sai ki tashi" daga haka ya nufi kofa, sauka tayi saman gadon ta tsaya na kusan minti daya har ta ji ba jirin kuma sannan ta nufi kofa a hankali kamar mai counting steps dinta ta bude kofa ta fita, tsaye ta gansa yana jiranta, ya mata wani kallo yace "Da kin bari na sake shiga office din ki gani" daga haka ya wuce ta bi bayansa, sallama yyi da co workers dinsa suka fita asibitin, a Wani pharmacy ya tsaya ya sauka ya siyo mata drugs da aka mata prescribing sannan ya dawo ya shiga motar suka bar wajen, sai da suka kusa gida a hankali tace "Yaya baxa ka siya min kaza ba plss" yace "A'a sai dai in siya maki akuya" murmushi tayi tace "Toh siya min" A waje yyi parking yace "Sauka..." Ta bude motar ta fita sai da ta shiga gate ya ga ledan maganin da ya siya mata" fitowa yyi motar rike da ledan ya wuce ciki da sauri, ganin har ta kusa apartment dinsu ya wuce nasu bangaren kawai, Babu kowa parlon, ya haura sama dai dai fitowar Anty dakinta tace "Ya jikin Imaan din?" Ya saci kallon kofar Umma kafin yace "Da sauki, Umma bata nan ne?" Anty tace "Ehh tun da ta ji kai ka kai Imaan asibiti ta fice gidan tun safe bayan ta gama bambaminta" Mujaheed ya xaro ido ya jingina da bango yace "Wa ya gaya mata Anty?" Anty tace "Abban ku, tunda ba tsoron ta yake ba" Ji yayi xufa na keto masa, Anty ta wuce ta bar sa wajen tsaye, da kyar ya ja kafafuwansa ya wuce dakinsa. Ammi ta hada ma imaan ruwan xafi a bayinta ta fito tace "Ga ruwan ki shiga, saura ki salance ruwan" Tashi Imaan tayi ta wuce dakin nata. Wanka Mujaheed yayi ya shirya jin lkcn Asr yyi yayi alwala ya fita gidan, yana dawowa masallaci dama part din inna ya nufa don Allah yasan yana tsoron haduwarsa da mahaifiyar tasa Inna ta fito daga daki jin an bude kofar parlor ganinsa tace "oyaa Alale, fitar min parlor kada in tara maka jama'ah, uban me ka xo min??" Mujaheed yayi dariya yace "Haba dai mai gidan kuma kike kora yau inna?" A fusace tace "Yana kabari, tun raina bai baci ba Mujaheed ka fita" Mujaheed yace "Abba ne fa yace kada mu tafi dake Inna" ta buda baki tana kallonsa tace "Kai haba?" Yace "Xan maki karya ne" xauna wa tayi tace "Ikon Allah, shi Ahmadun yace ku tafi ku bar ni kenan, to ya ma kansa kuwa, shine har da shi a bani hakuri da masu gadi a tsakar gida daxu, har hawaye fa sai da na xubar" Mujaheed yyi murmushi ya kwanta kan kujera, Inna tace "Toh ae shikenan, ya jikin Imaan din?" Yace "Da sauki" inna tace "Kuma da gasken bata da lafiya Mujaheed? Naga kamar don kar aje kauyen da ita yasa ta langwabe fa" Mujaheed yace "Ni dai akwai abinci?" Tace "Gashi can wanda Aisha ta kawo min ne daxu, bai wuce shinkafa da miya ba, Idan kuma biskit xa ka ci ga su can iri iri a daki wanda aka kawo ma Imaan, Kazan ma daxu na dumama na karasa cinyewa..." Mikewa xaune Mujaheed yyi yana kallonta na kusan second goma, can yace "Wa ya kawo mata?" shiru Inna tayi kanta a kasa, can ta saci kallonsa suna hada ido tace "Yo wa gareta banda Bukar??" tana fadin haka ta mike ta shige daki.... Imaan ta fi minti biyu tsaye bakin kofar bedroom din Ammi ta kasa shiga don bata san me xata ce mata ba, bude kofar dakin aka yi ta ja baya da sauri, Ammi ta dinga kallonta tace "Meye haka kike yi a bakin kofa ta?" Ta fara kame kame ba tare da ta kalli Ammi ba, Ammi tace "Imaan" daga kai tayi ta kalleta kamar xata yi kuka, Ammi tayi kasa da murya tace "Tell me what you want" tana jan fingers dinta a hankali tace "Ammi dama... Dama Sadeeq ne yace min yana waje ya xo gaisheni" Ammi ta dinga kallonta tace "Waye Sadeeq" ta sunkuyar da kai tace "Abokin ya Muhsin" Ammi ta yi shiru, can tace "Toh kar ki dade" Ta d'an yi murmushi tace "Toh nagode Ammi" daga haka ta saka Hijab dinta ta fito don tun da aka yi la'asar Sadeeq ke waje amma ta rasa yanda xata sanar ma Ammi ta fita, sosai hankalinta ya kwanta ganin ba motar Mujaheed a parking space, kamar mai tausayin kasa ta fita kofar gida, Tsaye ta ga Sadeeq jikin motarsa ya rungume hannunsa, as usual sanye da spec dinsa, dogon hancinsa da cute millionaires belt dinsa shine first abinda xaka fara noticing a fuskarsa daga nisa, Ta sunkuyar da kanta har ta isa inda yake tsaye, kallonta yake daga cikin glass din idonsa ko kiftawa babu, murya can kasa tace "Ina yini?" Yyi murmushin da ya bayyan dimples dinsa ya cire glass dinsa yace "Lafiya lau Imaan ya jikin?" A hankali tace "Na ji sauki" yace "Sure??" Ta gyada masa kai, yace "Toh Allah ya kara lafiya, hope kin sha dosage na afternoon, I mean ur drugs?" Ta gyada masa kai tace "Na sha" yace "Good, ya mama fa?" Tace "She's inside" ya langwabar da kai yace "Yaushe xan xo gaisheta pls" ta xaro ido tace "A'a xan ce kana gaisheta" cikin sanyin murya yace "Ke dai baki son yan gidanku su san ni koh?" xata yi magana aka bude gate, Inna ce tsaye bakin gate din tana kallon mai gadi tace "Kai iliya kake ko ilu, Kasan kan waya kuwa? Hadiza xa a kira min duk ba kowa gidan sai mai laluran can kuma nasan tana can tana bacci yanxu haka, yaran duk sun tafi kauye sai gobe xa su dawo" Imaan tayi stiff inda take bayan gabanta yayi mugun faduwa jin muryar inna, Mai gadin ya mike da sauri ya amshi wayar yace "Toh Hajiya...." Buda baki inna tayi tana kallonsa tace "Eh lallai baka da da'a, banda barbada kace ma matan gidan Hajiya nima kace min Hajiya, to bari kaji ko wa enda suka dauke ka aiki ma inna suke ce min balle kai, bar gani na haka xuciya mai kyau da rikon gaskiya da amana yasa ka gan ni har yanxu da kyau na, amma wllh da kyar idan ban girmi wanda ya haifi kakanka ba ma" yayi kasa da kai yana murmushi sosai yace "Yi hakuri Baaba tuba nake" inna tace "Kaji min yaro dai" Imaan dai ta kasa tsaye waje daya tayi backing din inna xuciyarta sai bugawa yake, murya can kasa Sadeeq yace "Ur grandmum?" ta gyada masa kai a hankali, kamar ance inna ta daga kai ta gan su, sake baki tayi ta kalli mai gadin tace "Kai wancan ba Imaan bace nake gani a tsaye?" Yace "Ita ce Baaba" Sadeeq yace "Let me go and greet her tunda ta gan mu" imaan dai kasa cewa komai tayi, ta ji kamar ta fashe da kuka, ae kuma shikenan.... Sadeeq na isa gun Inna dake ta kallonsa ya risina ya gaidata da ladabi, tace "Kai ne sabon saurayin nata?" Murmushi Sadeeq yyi ya kasa cewa komai, Inna tace "Ikon Allah, Kai ni fa na haifi ubanta Bukar, jikata ce fa, ita kenan Allah ya ba Bukar fa, a hannuna fa aka haifeta wllh, yanxu d'an nan da ban fito na gan ku ba shikenan, kai a garin ku haka ake yi?? ko bata ce maka kakarta na da rai bane, ita tunda bata da hankalin cewa ka shigo ka gaisheni kai baxa ka yi tunani ka shigo ba, dubi fa yanda ta ji kunya ta kasa juyowa kamar warce ruwa ya cinye" Sadeeq dai sai murmushi yake yace "Dama ai xan shiga in gaida ki kaka, kiyi hakuri" inna tace "Ni dai ba ruwana a dinga abu saboda Allah, tunda dai na kama ka mu je ciki" Yana murmushi ya bi bayanta suka shiga compound din ta rufe gate, tana nuna masa bangaren su Mujaheed tace "Kaga wancan katon ginin?" Yace "Na gani kaka" tace "Toh na wan ubanta ne, barrister suke ce masa, a India yayi karatun lauyancin sa, matansa biyu sai 'ya ya bakwai, Mujaheed shine d'an sa na fari, ina tsaye bakin kofar asibiti aka haifesa, yana nan xaka gansa wani lafcece dogo, da yake ada yana daga wannan karafunan turawan, to da kyar dai Ahmadu ya raba sa da su, nima na dinga rokon Allah har ya daina, a gabana fa ya girma, tun yaye yake wajena iyayen suka bar min, yana gama sakandari dama babansa ya biya masa kudin karatun likita a turai, ai ko in gaya maka babu irin fitsarar da bai koyo a can ba gaskiya, ni dai lkcn da ya dawo ma tsoron sa nake ga wani uban gashi da ya tara, buduwar da xai aura ma yar hayi ce, to sai kaninsa Yusuf, xaka gansa shi kuma wani lagwai lagwai kamar ya karye malam, da ma muka samu ya d'an yi kauri yanxu, sai kaga yanda aka haifesa d'an fiyot, to sauran kuma duk mata ne" Murmushi kawai Sadeeq ke yi yana bin inna, inna ta nuna masa part din su Imaan tace "Toh kaga wannan bangaren na su Imaan ne, Ubanta a can Habuja wajen neman abincinsa yake, ita kadai Allah ya basa a duniya, to dai ya fi babu d'an agwai da bak'in da, uwarta na nan wata bafillatana sai kirki, toh ni kuma kaga akurkin da suka gina min nake rayuwa ciki" ta fadi haka tana nuna masa nata part din. *The book Imaan is not free, you read for free ur cup of coffee*🤷🏻‍♀️ It's 300 via Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah Then u show ur evidence of payment via my WhatsApp digit 07087865788 to be included in the payment group._Am bringing this to the notice of my fans, idan xaku biya book din *Imaan* in dai ba digit din nan 👉🏻 07087865788 wato lambata kuka yi ma magana ba to Wllh ba ni kuka biya ma kudi ba, lambata guda daya ne kacal kuma gashi can a sama na rubuta, sannan ni bana amfani da wani kati idan ba Airtel ba, don haka duk wanda ya biya ta wani lamba daban wllh ya karanta hakkina without paying coz every page sai na sa number na da account number amma sai ku tsallake ku tafi kuna biya a gun wa enda ban sani ba ban san da su ba, ni kadai nake harkata a bangaren rubutu bni da wani xae ce ku tura masa xai turo min, talk to me directly through my WhatsApp digit 👉🏻 07087865788, su kuma masu siyar min da littafi har da hada document Billah na bar su da Allah, we shall surely meet in the hereafter in dai hakkina ne in sha Allah. Sannan masu *forwarding* ma su ci gaba there is power in the tongue_ Dariya Sadeeq yayi yace "Haba wannan ai ba laifi kaka" ta tabe baki tace "Mu je dai tukun" suna isa bakin kofa tace "To dai ka gani..." yana murmushi ya shafa kansa yace "Wannan ai ya fi duk sauran kyau kaka, ga shi ba hayaniya ba komai" Inna ta kara tabe baki ta bude kofar tace "Toh Allah ya masu albarka da suka gina min ai dai yafi babu" bin bayan ta yayi cikin parlon dake ta kamshin turaren wuta ta bude fridge ta dauko masa malt biyu da ruwan gora ta ajiye masa yace "Nagode sosai kaka" xaunawa tayi tana washe baki tace "Madallah, to ya sunan jik'an nawa?" Yyi kasa da kai yace "Sunana Abubukar Sadeeq" Inna ta gwalo ido ta saki wani kabbara da ya sa ya dago da sauri yana kallonta, tace "Yo ai sunan mahaifinta kenan Bukar, wllh shi ya haifeta, ai ko baka gansa ba mutumin kirki mai dattako da sanin ya kamata, sam yaron bai son 6acin raina, yo Ashe ma d'a na ne kai, to ka sha kurumin ka in dai wannan yarinya Imaan ce to wllh ka sameta ka gama ko taki ko ta so in dai ina numfashi kai ne mijin ba ruwana, don gaskiya ka kwanta min sosai, naga kana da hankali da nutsuwa" murmushi kawai Sadeeq yake, yace "Toh kaka idan ita bata ra'ayi fa?" Inna ta xaro ido tace "Wannan kuma ita ta jiyo ni dai ba ruwana, sunan ubanta fa gare ka kuma duk masu sunan an sansu da rikon aure, dubi fa yanda ubanta ya rike uwarta duk da rashin haifa masa yara da yawa da bata yi ba, to ni ko ina xan yarda ka kubce mata, A'a baxai sa6u ba wai bindiga a ruwa" Sadeeq yace "Toh nagode kaka naji dadi sosai" Tace "A'a ba xancen godiya, sunan d'a na fa gareka, ni dai ko yau kace xaka turo magabatanka kofa a wangale yake, to me xa mu ci da ita?? duk da dai ko sati ba ayi da aurar da yar uwarta ba amma idan ma iyayen nata sunce baxa su iya ba ni xan mata gado da kambodi da dirowa, Ina ce suna kenan kayan auren dai?" Sadeeq couldn't help it but laugh, tace "Kai ba xancen dariya bane, ni wlh sai in sa a siyar da filina guda daya in mata kayan daki, dama ni tsinannen bokon nan da ake yi yanxu ba d'ad'a ni da kasa yyi ba" Sadeeq ya sakko kasa yace "Da xa a ban ixinin turo magabatan nawa ba da jimawa ba da naji dadi sosai kaka" Inna tace "Wannan ai ba wata matsala bace bari Ahmadu ya dawo tunda kaga shi uban nata na Habuja" yace "Toh naji dadi sosai kaka" Inna tace "Kai don Allah... ai kuma an xama daya godiya ta me kuma, in ji iyayen ka a nan garin suke su ma?" Yyi kasa dai kai yace "Ehh suna nan" Inna tace "Toh dan siyasa ne uban naka?" Yana murmushi ya girgixa kai yace "Aa d'an kasuwa ne, Alhaji Ahmad Bulasawa ne Abba na" Inna ta xaro ido tace "Bulasawa?? Bulasawa dai da na sani na garin nan?" Bai dago ba still yace "Ehh shi" Inna ta bude baki tana kallonsa da kyau, can tace "Ikon Allah, ashe d'an babban mutum ne gabana ni Asabe, waye bai san Bulasawa ba duk garin nan da ma duk kasashen arewa, ba ance gidansa na nan nan GRA ba?" Yayi murmushi yace "Ehh" inna ta rike ha6a tana kallonsa tace "Ehh lallai ga kamanni kawai hanci ka fisa wllh, amma matansa aka ce biyu, to wacece uwarka a ciki, ko uwargidan? Don dai Bulasawa bai wuce Ahmadu na ba" Yace "Ehh ita" Inna tace "Atoh Alhmdllh, Allah na gode maka, kai abu sharr... bari Ahmadu ya dawo ko cikin watan nan ma ni gaskiya sai ka turo su Bulasawan, wa xai xauna" shi dai bai ce komai ba, Inna tace "Kai.... Allah mai iko, amma xan so kada wannan abun arxikin ya dau lkci gaskiya, ai aure abun arxiki ne" a hankali yace "Toh Allah ya sa haka kaka" tace "In sha Allah ya ma sa, ai abun arxikin xa a hada" Mikewa tayi tace "Bari in debo maka dambun namar da na ajiye ma Mujaheed" Da sauri yace "A'a xan koma ne kaka" Tace "Da wuri haka? Ni dai ka tsaya ko a leda ne sai in kulle maka" bata jira cewarsa ba ta shiga daki ba a dau lkci ba ta fito da gaba daya dambun naman a leda ta juye, ya xaro ido yace "Kaka wannan ai yayi yawa" tace "A'a ba ruwana ka amsa, dama Mujaheed da Imaan na ajiye ma to gaskiya ba rabonsu bane ynxu" dariya yyi ya karba yace "Toh ngd kaka, Allah ya kara girma" tace "Don ma dai duk sun cinye min cin cin din, kuma nasan ba kowa ya aikata min haka ba sai Maimoon da Ummi, ita Imaan bata daukan abu ba a bata ba sam ba halinta bane, gashi yarinyar bata da fitina tun tana jaririyarta, ga rashin yarda da kowa, lkcn ma ni har fargaba nake kada a kawota wajena don idan ta fara tsala ihu duk sai ta tara min munafukan anguwa an shigo min ana tambayar lafiya, me ya sameta?? dama Mujaheed kadai ne bata yi ma kiwa ba lkcn da take tashan kiwan, idan kuwa ta makalkalesa a lkcn bbu mai banbareta sai uwarta Aisha, ita ce ma ta makala masa yaya tun bata da wayo, in ko ba shi ya bata abinci ba dama abincin sai dai yyi ta galantoyi ba ci xata yi ba, in gaya maka lkcn Bukar na siyo mata wani runtumemen alawa idan ta saka a baki bata yrda ta ba kowa don rowa sai dai Mujaheed, shima din d'an dangwala masa xata yi a baki tana makale jikinsa, kai har goyata Mujaheed ya sha yi fa ta saki fitsari jikinsa sai dai ya canxa kaya, gaskiya ta takura ma Mujaheed ba kadan ba tana karama, shi sa in har yana gida uwar ta kawo ta bani da fargaba in kyalesu can su karata inyi ta kaina, to idan ban kyaleta ba ya xan mata tunda bata yarda da ni ta sa iyayenta su fara wani mugun tunani a kai na in shiga uku? A'a ba ruwana wllh" Murmushi kawai Sadeeq yake yana kallon inna, ta tabe baki tace "Toh gashi dai Imaan an girma kamar ba ayi ba, bari dai in bar ka haka naga kamar sauri kake, to sai yaushe kuma xaka sake shigowa??" yace "Ae ko da yaushe xan dinga shigowa gaida ki in sha Allah" Tace "Kai toh nagode yarona, Allah maka albarka, ya kare ka sharrin mahassada" ya mike ya ajiye mata dubu goma a gabanta yace "Ba yawa kaka a sa katin waya ayi xumunci" ta kauda kai da sauri tace "kai kai.... Ayi haka kuma Bukar??" Ya nufi kofa yana murmushi yace "Sai na kuma dawowa kaka" ta mike tana washe baki tace "Toh Allah maka albarka ka gaida min uwarka kaji?" Yace "In sha Allah xata ji" daga haka ya fita parlon just smiling, inna ta koma ta dau kudin tana kirgawa tana murmushi. Dama tunda inna ta shiga ciki da Sadeeq imaan ta wuce part din su ta fashe ma Ammi da kuka, Ammi ta mike tace "Lafiya?" Cikin kuka tace "Ko ba inna bace ta wani fito ta gan mu shine ta sa suka shiga ciki tare da shi, yanxu ban san dame dame xata fada masa ba, wayyo na shiga uku Ammi, nasan komai ma yau sai ta gaya masa" Ammi ta sake baki tana kallonta, ita kanta hango irin maganganun da inna xata juye ma Sadeeq yau ta dinga yi, can tace "Ae ko sai ki tashi ki tafi bangaren nata, idan ta ganki xata kama bakin ta" Imaan na girgixa kai tace "Ammi baxan iya ba, tun fa a gate ta fara basa labari" Ammi tayi jigum, can tace "Toh Allah ya kiyaye, ban san kuma me xan ce ba" daga haka ta bar parlon, Imaan ta dinga hawaye duk jikinta yyi sanyi babban damuwarta ma kada inna tace masa ai gashinta na nan bata son a gyara mata shi. Sadeeq na fita compound din yayi dialing number imaan yana murmushi, da sauri ta mike xaune tana kallon wayar, ta fashe da kuka a hankali ganin shi ne, da kyar ta daga kafin ya katse ta kai kunne, yace "Toh ai xaki fito mu yi sallama amma?" Tayi gathering courage tace "Me grandma dita ta gaya maka?" Yayi yar dariya yana wara ido yace "Ai babu abinda bata gaya min ba, she told me everything" Ta xaro ido kawai ta katse wayar ta fashe da kukan takaici, duk kiran da ya dinga yi kin dagawa tayi daga karshe ta shige daki ta kwanta kan gado bata fasa kuka ba. Bayan Isha jin ana knocking Ammi ta sa Hijab ta nufi kofar ta bude, Abba ta gani tsaye da Mujaheed ta ba su hanya tace "Ina yini Alhaji?" Ya shiga parlon Mujaheed na biye da shi ya xauna yace "Lafiya lau Aisha, ya mai jikin?" Xaunawa tayi ita ma tace "Da sauki Alhmdllh tana daki" Mujaheed bai yarda ya kalleta ba yace "Ina yini" tace "Lafiya" Abba yace "Ko bacci take?" Ammi ta mike tace "Anya kuwa...." Mujaheed dake tsaye dama bai xauna ba yace "Bari in dubata" Har xata dakatar da shi sai ta ji kunyar Abba, ta dai bi sa da hararan gefen ido don ko kadan bata so tafiyarsa dakin ba, murda kofar bedroom din yyi ya shiga ciki, tana xaune gaban mirror daga ita sai towel tana shafa lotion a duk jikinta, duk tunaninta Ammi ce ta bude kofar don bata ko kalli direction din kofar ba, jin shiru ta daga kai tana kallon kofar ta madubi, tsaye yake yana kallonta, suna hada ido yayi saurin dauke kansa, ta xaro ido tana gyara daurin towel din tace "Yayaaa" Mikewa tsaye tayi ta juyo tana kallonsa kafin tace komai calmly yace "Abba na jiran ki a parlor" bai jira cewarta ba ya fita dakin ta bi sa da kallo tana turo baki, Mujaheed na duban Abba yace "Tana xuwa abba" Abba yace "Ohk" Hijab ta sa har kasa ta fito parlon, ta gaida abba da murmushi fuskarta yace "Ya jikin mamana" tace "Abba ai na ji sauki" yace "Toh Alhmdllh, Allah kara lafiya" tace "Ameen" Abba yace "Ga watermelon nan you take much of it kin ji" a hankali tace "Toh nagode Abba, but...." Sai kuma tayi shiru, yace "But what?" Ta boye fuskarta tace "Abba ina son cin suya" Abba yace "Toh Mujaheed xai siyo maki yanxu" Mujaheed ya kalleta ta gefen ido irin kallon harara, Tana murmushi tace "Toh nagode Abba" daga haka Abba yyi ma Ammi sallama Mujaheed ma yyi mata suka fita. Abba yace "Idan mun fito part din inna sai ka tafi ka siyo mata, there is still time ai" Mujaheed yyi kasa da murya yace "Abba yanxu tare xa mu gun innan?" Yace "Of course, ban san urgent kiran da take min ba, it might even be something that isn't worth the call" Mujaheed yyi yar dariya yace "Dama xaka ga it's nothing that important...." Abba yyi murmushi yace "But we still have to listen, gudun matsala" Suna shiga parlon Inna ta shafe addu'ar da take kan darduma tace "Har ka iso kenan Bukar, to shi kuma wannan jelan da ya biyo ka fa?" Dariya Abba yyi ya xauna yace "Aa mun shiga duba mamana ne shine muka karaso nan din tare" tace "Atoh na gansa wani sandan sandan kamar basamude a bayanka" Mujaheed dai sae hararanta yake k'asa k'asa, tayi kasa da murya tace "Kana ji na Ahmadu?" Abba yace "Ina jin ki" tace "Kaga kujeran can da Mujaheed ya xauna?" Kai ya gyada mata yace "Na gani" tace "To wllh tllh a kai Bulasawa ya xauna" da mamaki Abba yace "Bulasawa kuma?" Tace "Eh, amma d'an sa ba shi din ba" Abba yace "Tohhhh.... a ina ya san ki?" Ta daga hannu da sauri tace "A'a ni bai san ni ba, a titi muka hadu yau kuma muka fahimci juna kwarai da gaske..." daga Abba har Mujaheed kallonta suka tsaya yi without blinking, can Mujaheed ya girgixa kai planning to get up and leave the parlor yaji tace "Ashe wai saurayin 'yar ka ce Imaan, amma algungumar bata ta6a sanar da ni ko da wasa ba, a wajen na gansu tsaye jikin santalelen motarsa, in gaya maka taji kunya tsamo tsamo da ta gan ni, ni dai ban kulata ba bakina a leko na taso keyarsa muka shigo cikin gida, d'an wajen Amadi Bulasawa mai gidajen man fetur sun fi dubu a arewa fa Ahmadu" dakatawa Mujaheed yyi da sauri ya juya yana kallonta, Abba na gyada kai yace "Tohh da kyau hakan" Inna tace "Kai fa kasan da kyau yaro, wato idan Allah yyi auren har kasan waje fa sai an fitar da ita an juye duk gurbatattun jinin jikinta dake ja mata lalura a sauya mata sabo, sannan kasussukan jikinta su ma duk sai an ce xa a sauya su ta rabu da ciwace ciwace na har abada, kasan fa bbu abinda turawan nan basa iyawa in dai da naira, to ga naira dai faca faca ta samu, ae ni bayan fitarsa sai da nayi ya ma ake kiran sujjadar nan na godiya ga Allah?? To ni dai nayi wllh kuma na dade goshina a kasa" Dariya kawai Abba yake yana kallon mahaifiyar tasa, Mujaheed dae sai juya counter din hannunsa yake, inna ta marairaice tace "Ahmadu ka rufa min asiri ba abun dariya bane wannan, sannan yaron fa duk ya damu wai xai turo magabatan sa nan ba da dadewa ba ayi xancen aure, kasan su kuma manyan mutane basa son kwalo kwalo kada a bari wannan yaron ya kubce ma jikata in shiga uku gaskiya" Juyawa Mujaheed yyi ya dinga kallonta, Abba yace "Haba maganar aure kuma Inna, ko secondary fa bata gama ba" Inna ta wani tsuke fuska cikin d'aga murya tace "Allah ya tsine ma sakandarin, sakandarin banxa ga abun arxiki kana xancen sakandari, ko a gidansa wllh xai bari ta karasa, baka gansa ba dogo yanda kaga wannan mutumin dake kusa da kai a xaune, shi ma da kyar idan baya daga karafunan nan na turawa don kirjinsa duk a tale, kana ganinsa kaga d'an boko don gilashi ne ma a idonsa, toh irin wannan ne baxai bari ta karasa sakandarin jaraban ba idan anyi aure, gaskiya Ahmadu ku maida hankalin ku sosai a kan maganar nan da nake gaya maka, wllh kullu yaumin fargabana mijin da Imaan xata aura tunda ga yanda Allah ya halitto ta, mai rufin asiri kadai baxai iya da lalurorinta ba sai hamshakin mai kudi, da yau ace Bukar ya tara yara kamar yanda ka tara to fa da imaan bata kai labari ba don nasan ba xai tara uban kudin da xai dinga kashewa kan ciwonta ba, to astagfirullah kaga amfanin haihuwan kadan ba da yawa ba, to yanxu dai ga yaro matashi kyakkyawa d'an masu kudi ya fito, bari ma kaga abinda ya ban Ahmadu" *The book Imaan is not free, you read for free ur cup of coffee*🤷🏻‍♀️ It's 300 via Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah Then u show ur evidence of payment via my WhatsApp digit 07087865788 to be included in the payment group.cewa komai ba ma coz I know I have Allah_😍 Mikewa inna tayi ta dauko kudin da Sadeeq ya bata a daki tana murmushi tace "Dubu goma ce ciff, babu yanda banyi da yaron ya bari ba ya ki, toh ni ko xan tsaya muna jayayya da shi ne, haka dai na hakura na amsa" Mujaheed ya kasa daina kallonta ko kiftawa babu, Abba ya sauke ajiyar xuciya yace "Toh Allah ya saka da alkhairi" inna tace "Toh ya xancen turo magabatan nasa fa?" Ya d'an yi shiru sai kuma yace "Inna da dai a jira Sadeeq ya dawo koh?" A fusace inna tace "Oh oh Allah waye kuma Sadeeq?? dole sai Bukar din yana nan? kai ba mahaifi kake wajenta ba, Bukar da idan ya tafi Habuja kamar baxai sake dawowa ba, ni ba ruwana ka kirasa a waya ka gaya masa komai in ma ya kama ya taso ne ya taso kawai, to nasan bayan shekara nawa xai dawo idan muka tsaya jiransa??" Abba ya dinga gyada mata kai nan ko neman abinda xai ce mata yake, can dai yace "Toh ko xa ki kirasa da kanki Inna??" ta tsuke fuska tace "Baxan kira ba idan baxa ka kira ba a bar kiran, iyaka in shirya in tafi kano gun kawun ku ya amshi gaisuwa da kudin auren kawai, ai ba ku kadai ke da iko da ita ba" cikin low voice Mujaheed yace "Meyasa baki maganan wa enda suka girmeta a gidan sai ita??" Inna ta masa wani kallo tace "kana nufin su ku kenan masu tambadewa a titi, wato kai da Isuhu, to ni meye ruwana da rayuwarku fisabilillahi? Da ku yi aure da kar ku yi duk daya wllh tunda baku da mafada, ko ni na ajiye ku da xan maku magana idan ba rainin wayo ba, ko me na hada da ku? Ga dai iyayenku suna kallonku basu ce komai ba sai ni bare? Imaan dai Allah ya fiddo mata zankadeden miji in sha Allah, to ni na ajiye ku da xan maku magana idan ba rainin wayo ba, ko me na hada da ku??" Abba ya mike yyi kasa da kai yace "Toh ina fita ynxu xan kira Sadeeq din" Inna tace "Gwara haka dai, kana kiransa ka zayyane masa duk abinda nace tass, kace masa yaron ma takwaransa ne shi ma Sadeeq ake ce masa, baka gansa ba Ahmadu kyakkyawa ga hanci kamar an xana biro, ga idanuwa maa sha Allah" sai da safe Abba yayi mata ya nufi kofa Mujaheed ya bi bayansa, inna ta bi Mujaheed da harara tace "Oho dai bakin cikin ka xai kare maka Mujaheed, daga jin kanwarka tayi miji sai bakin ciki ya bayyana karara a fuskar ka? To aniyar moda ta bi randa, imaan dai nan gani nan bari" Shi dai bai tanka ta ba har ya fita ya kulle kofar. Abba na fita ya shiga kiran d'an uwan nasa, daddy na dagawa ko gaisawa basu yi ba yace "Toh tsohuwa dai ta 6aro mana wani babban aikin Sadeeq" Daddy yace "Tohhh, Me kuma ya faru" Abba yace "Wai aure take son ayi ma Imaan" Daddy ya wani bude ido da mugun mamaki yace "Aure kuma Barrister?" Abba yace "Wllh, and she is damn serious, kawai kirana tayi daxu tana nemana shine na taho and this is what she said" cike da confusion Daddy yace "Aure fa kace Barrister, toh ita tayi mata mijin?" Abba yace "Na dai ji tana ta xancen d'an gidan Bulasawa, ban san ko ita Imaan din ta ma san sa ba, I tried telling her she is too young ko secondary bata gama ba but inda inna take shiga ba nan take fita ba, she didn't even give me a listening ear, she so mean it, so ko xaka kirata yanxu??" Daddy yace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un me yasa inna take haka" Abba yace "Kaga gobe Friday if you can squeeze up things ka taho sai mu san yanda xa mu yi koh? Ni bana son in ja xancen ne ranta ya baci kasan yanda take abubuwanta, shi sa mata sallama kawai na fita" Daddy yace "But ka fa san idan tayi deciding abu it's hard ta canxa barrister" Abba yace "Don't worry, ka dai taho goben sai mu san abun yi in sha Allah" Daddy yace "Toh Allah ya kai mu" sallama suka yi Abba ya kalli Mujaheed da kansa ke kasa yana tafiya absentmindedly, Abba ya dafa shoulder dinsa yace "Are you okay son?" Kallon Abba yyi da sauri, sai kuma ya d'an yi murmushi yace "Sure Abba, kawai dai har yanxu I am surprise at what grandma is planning" Abba ya sauke ajiyar xuciya yace "Imaan din har nawa take ma banda abun inna, ga shi ba wani lafiyan kirki gareta ba, inna dai kam abun ta gaba yake ba baya ba, ita kawai ayi auren saboda d'an mai kudi ne, Allah ma kadai yasan abubuwan da ta fada ma yaron, tun tasowar mu muke fama da ita a haka muna ta lallabawa dai, gashi bbu abinda ya canxa har yanxu, abu kuma ya xo ya hade da tsufa, sai dai mu yi ta mata addu'a, Allah kuma ya rabamu da ita lafiya, amma abinda ya ban mamaki shine ta yanda ta san yaron, kuma anya Imaan ta ma san sa kuwa?" Mujaheed dai bai ce komai ba sai pressing din counter dinsa yake a hankali, Abba yace "Kai kasan yaron Bulasawan da take fadi?" Mujaheed ya girgixa kai, bayan few seconds yace "But ina ga Yusuf baxai rasa sanin sa ba don yana mingling da irin su" Abba yyi murmushi yace "I will call and ask him" suna isa sashinsu, Abba yace "Don't forget ka fita ka siyo mata naman da tace" a hankali yace "Toh" motarsa ya bude don makullin na hannunsa ya shiga, Abba kuma ya shiga cikin gida, Mujaheed ya ja motar ya fita compound din. Mujaheed na dawowa daga siyo Tsiren da Abba yace ya nufi part din su Imaan, a hankali ya kwankwasa kofar sannan ya murda yaji a bude, shiga parlon yyi, ya sauke idonsa bayan sun hada ido da Ammi yace "Gashi Abba yace a kawo mata" Ammi ta kwalo ma Imaan kira don tana bedroom dinta, ko me ta tuna sai kuma ta mike xata amshi ledan sai ga Imaan ta fito sanye da kayan barcinta, xata shigo parlon Ammi ta dinga mata wani kallo, da sauri ta juya ta koma dakin ta rufe kofar, Ammi ta karbi ledan ta nufi dakinta ba tare da ta amsa sai da safensa da ya mata ba, juyawa yyi ya fita parlon ya kulle kofar. Washegari daga Imaan har Ammi suka yi mamakin xuwan Daddy ba notice, Bayan Daddy ya shiga bedroom Ammi ta bi bayansa, xaune ta samesa gefen gado tace "Yallabai xuwa babu notice, hope lafiya dai" Yace "Ehh I came for something urgent, xuwa lahadi xan koma in sha Allah" tace "Allah ya kai mu" shiru yyi hakan yasa tace "A kawo maka breakfast ne?" Yace "Noo, Ina son maki wani tambaya, Imaan tana da wani ne dake nemanta?" Ammi tayi shiru tana kallonsa a bit shocked, can tace "Lafiya Yallabai?" yace "I am asking you..." girgixa kai Ammi tayi, she have got no option then to protect her daughter, a hankali tace "Not at all, ita da bata xuwa ko ina daga boko sai islamiyya, is there any problem" yace "Ohk" mikewa yayi ya shiga bathroom ita kuma ta fita a sanyaye tana mamakin tambayar, to me kuma ya faru, tana fita parlor tayi still don sai a sannan ta tuna abinda Imaan tace inna tayi jiya, wato har inna ta kirasa kenan ta gaya masa, daki ta tafi gun Imaan, tana kallonta tace "kin ga abinda nake guje maki ko, to ina jin inna ta kira Daddyn ki har ta fada masa xancen yaron jiya, without any doubt abinda ya dawo da shi kenan" Imaan ta xaro ido a tsorace tace "Daddy ya maki maganan ne?" Ammi tace "Dama tun ba yanxu ba nace maki ba ruwana kar ki ja min matsala, gaskiya sai ki san abinda xa ki ce ma Daddyn ki, don't involve me in this" daga haka ta fita dakin, imaan ta kasa xaune waje daya gabanta ya dinga faduwa hawaye cike idonta, daga karshe ta fice a dakin, direct part din inna ta nufa hawaye cike idonta.... shigar Mujaheed parlon kenan ya je gaisheta daga inda yake tsaye, ko amsa gaisuwarsa bata yi ba tana kada shayi a kofi tace "Ni fa Mujaheed tsabar yanda nasa maganar jiya a rai har mafarkinsa sai da nayi wlh, wai ga Imaan a daula iya daula babu abinda babu a runtumemen gidan na more rayuwa, har naje masu sati biyu, in gaya maka yau... a kawo min kaji, gobe.... a kawo xabee, gata... a kawo kwayakwayay, citta... a kawo tika tikan Kifaye, ga gwangwanin madarana da bournvita da suga an min dak'en da shi a daki, nayi wani jazur da ni sai sheki nake malam, Shi ko bulasawan kullum xai fita sai ya ajiye min dubu biyu in sa kati, wllh tllh ba karya nake maka ba Mujaheed" Mujaheed dai na tsaye daga bakin kofa yana kallonta, ta tabe baki ta yagi bread ta kai baki tace "Ni dai ba ruwana, Ahmadu ya shigo in san yanda suka yi da Bukar din" Jin an bude kofa Mujaheed ya juya, imaan ta shigo ko takalmi bata cire ba, tana kallon inna kamar xata fashe da kuka tace "Inna me kika ce ma daddy na?" Inna tace "Waye kuma Daddyn ki?" Imaan tace "Wai ni nace maki wanda kika gan ni da shi jiya saurayina ne??" Inna ta kyabe baki tace "Kya ji da shi, ni dai baxan kula ki ba ki xageni, na riga na gama maganata, wllh Mujaheed baka ga yanda ta ji kunya ba jiya da ta gan ni kamar fa ta nutse, ni dai ban bi ta kanta ba ban kuma kulata ba bakina a leko na ja Bulasawan muka shigo ciki, to kuma meye xata shigo min ta tale baki kamar wata agwagwa? Ni dai ba ruwana" Mujaheed ya juya ya fice daga parlon... imaan ta durkushe wajen tana kuka sosai tace "Wllh idan kika sa Daddy ya min fada ko ya dokeni ni dai Allah na kallon ki Inna, ni ban ce naki saurayina bane, abokin yaya Muhsin ne ni ban san shi ba" Inna dai na ta cin bread dinta tana shan shayi, Imaan ta gaji da kukanta ta mike xata fita inna tace "Toh aniyar ki dae dama ya bi ki a baya, ba ruwana. Ni nasan wani yaya Muhsin" imaan bata tanka ta ba ta fice hankali tashe. Tsaye Imaan ta ga Mujaheed dai dai inda xata sha corner xuwa part din su, xata gudu ya kamo hannunta, a tsorace tace "Wayyo yaya don Allah kayi hakuri inna sharri take min...." Fingers biyu ya daura kan lips dinsa yana mata wani kallo, haka yasa tayi shiru tana kallonsa gabanta na faduwa, ya nuna mata dakalin dake wajen fuska daure yace "Xauna" Ba musu ta xauna kamar xata fashe da kuka, yace "What did I tell you about standing outside with guys?" Hawayen dake makale idonta ya gangaro tace "Don Allah kayi hakuri yaya" yace "Me yasa baki jin maganata?" Tace "Ina ji fa yaya" yace "Toh meye tsakanin ku da mutumin?" Ta girgixa kai da sauri tace "Ba komai, abokin yaya Muhsin ne?" Yace "Me yake xuwa yi wajen ki?" Ta sunkuyar da kai ta rasa abun cewa, strictly yace "Answer me now before I give you an unclean slap" Ta fashe da kuka a hankali tace "Ba komai fa yaya, kayi hakuri plss" dauke kai yyi na few seconds, sai satan kallonsa take, ganin yanayinsa gabanta ya tsananta bugawa, can ya kalleta ya durkusa gabanta calmly yace "Abba da daddy xa su kira ki su tambayeki what's between you and the guy, me xa ki ce masu?" Ta sauke idonta a hankali tace "Xance masu abokin yaya Muhsin ne" Ya wani hade rai yace "No, kalleni da kyau" Daga kai tayi tana kallonsa, sosai gabanta yyi mugun faduwa, a hankali yace "You tell them babu komai tsakanin ki da shi, kin ji ni?" Ta gyada masa kai kawai, yace "Good, ko baki son ki gama karatu kamar Seeyama? Baki son ki tafi university" Ta turo baki ta boye fuskarta da hannunta murya can kasa tace "Ina so mana yaya" Jin bai ce komai ba ta xame hannunta a hankali ta ga kallonta yake, dauke idonsa yyi murya can kasa yace "Idan ma yace son ki yake kice masu ke baki sonsa" Yar dariya tayi, ya jefa mata wani kallo xai yi magana sai ga Abba da Daddy xa su part din Inna, mikewa yyi da sauri, Daga Abba har daddy kallonsu kawai suke, Mujaheed yyi kasa da kai yana gaida daddy, daddy ya amsa da murmushi yace "Ya aiki Muhammad" Mujaheed yace "Alhmdllh" Abba yace "I called ur line baka daga ba" Mujaheed yace "Na bar wayar can daki naje gaida Inna ne" Abba yace "Ohk" a hankali Imaan ta gaida Abba ba tare da ta yarda ta dago kanta ba, Abba ya amsa daga haka suka wuce tare da Daddy da ko kallonta bai sake yi ba, mikewa Imaan tayi tana kallon Mujaheed, I yace "Kin ji abinda nace maki koh?" Kai ta gyada masa a hankali, daga haka ya wuce ya bar ta wajen a tsaye, Mujaheed bai karasa part din su ba mota ta shigo gidan, Driver na parking Umma ta fito, suna hada ido gabansa ya fadi sosai ya juya da sauri to make sure Imaan bata biye da shi a baya, driver ya sakko motar ya xaga ya bude booth, set biyu na boxes masu d'an karen kyau da tsada ya fiddo a booth din yyi cikin gida da su, Tuni Umma ta wuce ciki ita ma, Mujaheed ya bi su da ido. Tare Abba suka shigo parlon da Daddy, Inna tace "Naji dadi da ka ba lamarin nan muhimmanci ka taho Bukar, ina fatan kuma kayi murna da jin wannan abun arxikin?" Daddy yace "Ina kwana" tace "Lafiya lau, ya ka xo?" Yace "Alhmdllh" tace "To madallah" Daddy yace "Jiya Barrister ya min bayanin komai...." Ta washe baki tace "Toh Alhmdllh" yayi kasa da murya yace "Amma inna, Imaan yarinya ce sosai sannan ga ta ba lafiyayya ba...." Inna ta katse sa tana kallon Abba tana nunasa tace "Kai dai wllh Ahmadu baka yi ba, yanxu sai da ka xugesa sannan xaku shigo min nan?" Daddy yace "Aa baki fa jira na kai aya ba inna" mikewa tayi a fusace tace "Babu wani xancen kai aya Bukar, ni kai da d'an uwanka xaku munafurta daga taimako, ni xa ayi ma cin dunduniya, waye baya son nasa ya huta a xamanin nan, koko xan ma Imaan xa6in da xae cuceta ne ko ance maku ban san abinda nake bane, ku kuka haifeni ko ni na haifeku, to wai ma ku tsaya tukun, wai idan aka yi auren nan tare za mu tare gidan da ita?? duk girman gidan naga dai nata ne ita kadai ba tare da ni xata more rayuwar xaman gidan ba, iyaka bai fi a sati inje sau biyar ko shidda ba, to idan baku aurar da ita ba jik'a ta xa kuyi ku shanye ko enlargement xa ku yi da ita kuna kallo a parlor, yau naga abinda ya isheni bai ishi ubangijina ba" Daddy yace "Kiyi hakuri, bai kai haka ba inna, sai ki hada mu da yaron ayi magana ta fahimta" Inna ta goge xufan da take yi tace "To yanxu naji batun kirki, sai dai kuma ban san inda za a samo sa ba, amma ita imaan din ai baxata rasa lambarsa ba, ku kira ta ta taho a kwashe min a wayata in kirasa" Abba dai sai kallon mahaifiyar tasu yake, Daddy ya ciro handkerchief din aljihunsa ya share xufar goshinsa, Abba ya sauke wani boyayyen ajiyar xuciya yace "Toh xa a amshi lambar nasa a gunta in sha Allah" Inna tace "Toh idan kun kirasa me xa ku ce masa?" Abba ya d'an kalli daddy, Daddy yace "Ce masa xa mu yi ya turo magabatan nasa" Inna ta xauna kan kujera tana murmushi tace "Toh Allah maku albarka, ya buda maku" mikewa Abba yyi, daddy ma ya mike yace "Toh anjima xa mu shigo in sha Allah" tace "Toh shikenan amma kar fa ku ce xa ku ja lokacin don yaron yace a matse yake yyi auren" Babu wanda ya tanka ta cikinsu har suka fita parlon. *Abba na kallon Daddy yace "Kada kayi ma Imaan magana tukun, I want to confirm who the guy is from Yusuf, Mujaheed yace baxai rasa sanin sa ba" Daddy yace "Toh shikenan, amma I will so deal with her, ita har nawa take xata fara kula samari can you imagine?" Abba yace "Nace kar kace mata komai tukun, ni nasan abinda xan yi" Daddy bai iya yace komai ba, don gaba daya ransa ya gama baci, suna isa part dinsa ya shiga, Abba kuma ya karasa nasa part din. Direct bedroom din Mujaheed Abba ya tafi ya bude kofar, Mujaheed na xaune tare da Umma a dakin ya sunkuyar da kai yana saurarenta, Umma na ganin Abba tayi shiru daga abinda take cewa, Abba yace "Ka sameni parlor Muhd" a hankali Mujaheed yace "Toh Abba" daga haka ya rufe kofar, Umma tace "Wai me ke faruwa, jiya naga mood dinsa gaba daya sai a hankali, halan tsohuwarsu ce ta tada wani fitinar?" Murmushi Mujaheed yyi yace "Ehh.." Umma ta buda ido sosai tace "Wai me take so?" Kamar Mujaheed baxai ce komai ba sai kuma yace "So take ayi ma Imaan aure" Umma ta xauna da kyau da mamaki tace "Aure kuma? imaan din saurayi gareta da xa a mata aure? Ko tana da yaron da xata hada ta da shi ne?" Mujaheed ya d'an yi shiru sannan yace "Ban sani ba Umma" Umma ta hade rai tace "Baka sani ba duk kusancin ka da inna, ko dai gaya min ne baxa ka yi ba??" Ya girgixa kai yace "Umma ni bata gaya min komai a kai ba" Tuni mood din Umma ya canxa, Mujaheed dai kallonta kawai yake, Tabe baki tayi tace "To ma gani ai, yanxu dai xaka yi transfer din ne ko Safeenar xaka ma?" A hankali yace "Anjima xan maki Umma" ta mike tace "Toh ina jira" daga haka ta nufi kofa ta fice dakin, Dafe kansa yyi na kusan minti daya, can dai ya tashi ya tafi parlon Abba. Abba na kallonsa yace "Mun gama magana da Yusuf yanxu a waya yace bai san yaron ba, so what I want you to do now is ka samo min number sa a wajen Imaan, but ita kanta bana son ta san ka dau number yaron, do it wisely" Shiru Mujaheed yyi, Abba yace "Yea just get his digit by any means without her knowledge" Yace "Toh Abba" Abba yace "I want it before the end of today" yace "I will do that in sha Allah" Abba yace "Xaka iya tafiya if u have anything doing" mikewa yyi ya fita, Umma ya gani sanye da Hijab ta rike purse ta nufi kofa, ko lura da shi bata yi ba har ta fita, ya bi ta da kallo sannan ya wuce sama . Imaan na xaune kitchen tana kallon Ammi dake kwashe girkin da tayi a warmer, Ammi tace "Kafin Magrib idan ban dawo ba sai ki kai mata" Imaan dai bata ce komai ba, bayan Ammi ta gama tana kallonta ta marairaice tace "Ammi amma me yasa baxan bi ki ba plss" Ammi tace "Nace ki bari lahadi idan kin dawo islamiyya kije, yanxu akwai mutane da yawa a gidan you will be uncomfortable" a hankali tace "Toh Ammi" Ammi ta fita kitchen din ta mike ta bi bayanta, Hijab Ammi ta sa ta shiga parlor gun daddy tace "Yallabai xan je xa mu amshi lefen Halima" Daddy yace "Ohk xan je cikin gari dama, let me drop you" Imaan ta turo baki ganin ita kadai xa a bari gida, kamar xata yi kuka tace "Daddy in raka ka?" Wani kallo da ya tsorata ta ya maka mata yace "You are stupid" sunkuyar da kanta tayi ta juya ta wuce daki, Ammi ta hade rai tace "Ni ban gane haushinta da kake ji ba tun daxu, ka kuma ki gaya min me ke faruwa" Yace "Madam dauko min makulli a daki and stop questioning me" daga haka ya fita parlon, tabe baki tayi ta tafi ta dauko masa makullin, dakin Imaan ta leka ta ganta xaune gefen gado tace "Ki tashi kiyi sllh sai ki sa kallo ko a daki ne kiyi" daga haka ta rufe mata dakin, kusan tare suka Isa parking space da Mujaheed, kansa a kasa ya gaida Daddy, daddy ya amsa yace "Ya aikin?" Yace "Alhmdllh, xa ku fita ne Abba" Daddy yace "Ehh xan je cikin gari ne" Ammi ta hade rai ta bude front seat ta shiga, Mujaheed dai bai yarda ya kalleta ba dama, daddy yace "Toh sai na dawo" Mujaheed yace "Toh a dawo lafiya Abba" daga haka ya bar wajen yana d'an murmushi, dama tun safe yake tunanin yanda xai hadu da Imaan har ya dau lambar Sadeeq, kan farin kujera ya tafi ya xauna har Daddy ya fita gidan, bayan kusan minti biyar ya mike ya nufi part din nasu, murda kofar yyi a hankali ya shiga ciki yana kallon parlon ya ga bata ciki, ya jawo kofar ya rufe ya nufi bedroom dinta, tsaye yyi bakin kofar kafin ya murda gently ya tura kofar, bai ganta dakin ba ya d'an yi jim, running tap ya ji a bathroom ya gyada kai, ya tafi gaban madubi ya dau wayarta dake ajiye xai yi silencing wayar yaga ma a silent yake, ya xura a aljihu sannan ya karasa kofar bayin ya makale jikin bango, Imaan ta gama alwalan da take ta bude kofar bathroom din ta fito, ji tayi an cafketa ta baya, ta fasa wani ihu a raxane ya jawo ta jikinsa ya riketa gam, kafin ma ya kai ga cewa komai ta gane shine saboda scent dinsa, k'asa cewa komai tayi ta dinga numfashi a tsorace don tayi mugun tsorata, bayan few seconds numfashinta ya dawo dai dai, juyo da ita yyi yana kallonta yace "Anjima Abba xai kira ki, kin dai ji abinda nace maki daxu koh?" Kin cewa komai tayi, ya hade rai yace "Ba magana nake maki ba" tace "Naji mana" Saketa yyi ya nufi kofa, ta murguda baki tace "After all he is just a frnd, and he is...." juyowa yyi da sauri yana kallonta, tayi maza ta shige bathroom ta sa key. Mujaheed ya koma inda yake xaune ya fiddo wayar nata a aljihu ya shiga call log, bai ga wasu calls ba sai na Daddy sai wani number da bata yi saving ba, ya dinga kallon Number kafin yyi dialing, katsewa aka yi sai gashi an kira, ya daga ya kai kunne yyi shiru, daga daya bangaren Sadeeq yayi sallama, Mujaheed ya cire wayar a kunnensa ya katse kiran ya ciro wayarsa ya kwashe number sannan ya danna ma number block ya goge log din kiran a wayar gaba daya. Imaan na idar da sllh ta debo chocolates ta xuba su kan gadon ta sannan ta kunna kallo ta kwanta tana shan chocolates tana yi, ta fi minti talatin tana kallo ta tuna Sadeeq ya kira ta tun daxu bata dauka ba, mikewa tayi xaune da sauri tana kallon gaban madubinta don nan ta ajiye wayar, da mamaki ta karasa wajen mirror din idonta a kan inda ta bar wayar ganin babu shi, lkci daya Mujaheed ya fado mata, ta xaro ido tana fatan ba shi ya dauka ba, duba dakin ta shiga yi amma ba alamar waya, kamar xata yi kuka ta dau Hijab ta sa ta fita, bata tsaya ko ina ba sai part din su, Babu kowa parlon gidan tsit don har sannan su maimoon basu dawo ba duk da ta ji alamar akwai mutane a kitchen, ta wuce sama cikin sanda tana waige waige, tana ta tsaye corridor tana kallon kofar dakinsa, karasawa tayi ta murda kofar a hankali ta tura, ba kowa dakin sai kamshi me dadi dake tashi, ta karasa ciki da sauri tana kalle kallen dakin, wayarsa ta gani gefen gado amma bata ga nata ba, dauke wayar tayi ta boye cikin Hijab ta fita da sauri, da gudu ta karasa part dinsu ta shige parlor ta sa makulli tana turo baki, xaunawa tayi tana kallon wayar ta bude taga ba lock, gallery ta shiga ta ci karo da hotan Farida a WhatsApp images, ta shiga wajen, duk yawanci hotunan farida ne ta ajiye wayar ta kunna TV nan parlor ta kwanta kan kujera ta ci gaba da kallonta. Mujaheed na kallon agogon wrist dinsa yace "Aunty xan wuce aiki yanxu..." Aunty dake hada stew tace "Toh Allah ya kiyaye" fita yyi daga kitchen din ya wuce sama ya shiga dakinsa, makullin mota ya dauka ya kara feshe jikinsa da turare, ya juya xuwa saman gado xai dau waya yaga babu, da mamaki ya dinga kallon inda ya ajiye wayar, ya fito ya duba dakin Aunty ko ya mancesa a ciki ne yaga babu, fitowa yyi daga dakin yana sauka stairs yyi still a zuciyarsa yace Imaan, to yaushe ta shigo?? karasa sauka yyi ya fita parlon dai dai shigowar daddy compound din da mota, a hankali yace "Shit" Ya tsaya har Daddy ya fito daga motar, ganin leda a hannunsa ya karasa da sauri ya amsa yana masa sannu da dawowa, daddy yace "Thanks Muhammad, Barrister ya dawo?" Mujaheed yace "A'a bai dawo ba" a tare suka karasa apartment din Daddy dake amsa call da ya shigo wayarsa, Daddy yyi knocking, Imaan dake kwance ta mike xaune da sauri tana xaro ido tace "Waye wannan?" Daddy yace "Open the door" tashi tayi ta bude kofar, Daddy ya ci gaba da wayar da yake, ta wani xaro ido ganin Mujaheed ta juya da sauri ta koma ciki, Mujaheed ya saci kallon Daddy sannan ya shiga, Har ta dauke wayar nasa da ke ajiye kan kujera xata gudu ya fixgota, ba daman tayi ihu hakan yasa ta gatsa masa cixo a hannu da duk strength dinta, ba shiri ya saketa, da gudu ta nufi dakinta, sai a kan idon Daddy da ya shigo ya dinga kallonta da mamaki yace "Zo nan Imaan, whats wrong with you?" Kamar xata yi kuka tace "Daddy yaya ne" Mujaheed ya kasa daga kai ya ji kamar ya nutse a wajen, Yyi saurin ajiye ledan hannunsa yace "Abba xan wuce gun aiki" bai jira cewar daddy ba ya nufi kofa ya fita. Da Magrib imaan ta tafi kai ma inna abinci bayan ta sake boye wayar Mujaheed da kyau, duk kiran da aka dinga masa na Farida kawai ta daga, tun da ta fito compound dama gabanta ke faduwa, da sauri sauri ta karasa part din Inna, Yusuf ta gani xaune, ta wara ido ta ajiye abincin hannunta tace "Lahh ya Yusuf yaushe ku ka dawo?" Ya kalleta ya d'an yi murmushi yace "Daxu..." Inna tace "Baki ga da ya shigo ba daxu duk a kode wllh, ai yanxu ya washe a haka, Allah ya rufa ma ke da Mujaheed asiri ba ku je ba, baku da rabon wahala, amma wannan garin ae ba wajen xuwa bane tirr" Imaan ta duka kusa da shi tana dariya tace "Toh me ka kawo min ya Yusuf" ya shafa kansa bai ce komai ba, Inna tace "Yauwa ina maka xancen kirki kafin wannan mata ta shigo..." Ya sauke ajiyar xuciya a hankali yace "Ae ina ji" tace "Ko kai ya ka gani, wannan ba shawara mai kyau bace na kawo?" Da kamar baxae ce komai ba sai kuma yace "Da dai kiyi hakuri a bar xancen inna...." Ta katse sa da sauri tana gwalo ido tace "Xancen auren?" Calmly yace "Ehh" inna ta saki baki tace "Ehh lallai kai da Mujaheed kun xama abun tsoro, yanxu har kai isuhu bakin ciki kake ma yar uwar taka? Anya 'ya yan Ahmadu xa ku ga annabi kuwa? Ba kunya ba tsoron Allah ku fito kiri kiri kuna nuna ma yar uwar ku bakin ciki" Shi dai kallonta kawai yake, imaan ma sai kallonta take don bata gane kan xancen ba, Inna na tabe baki tana girgixa kai tace "Har abada in dai ni yar halas ce ba ni ba shawara da gantalallu irin ku, tun da haka ku ka xama gwara in yi ta kaina, to wai tsaya idan aka ki gabatar da ita jika ta xa mu yi mu baku ku shanye?" Nan ma dai bai ce mata komai ba, ta rike ha6a tace "Ai ni na shiga uku, lallai 'ya yan Ahmadu mugaye ne, sam ba alheri a ranku, to wai tsaya... ku xa ku aureta idan aka bar xancen?" Ya kalleta yace "Kika sani?" Imaan da ta fara dago xancen ta wani hade rai xata mike ta bar parlon Inna ta riga ta, tana kallon Yusuf cikin rashin hankali tace "Ku har kuna da kudin da xa ku rike min jikata? Ku a su wa kuma Allah na tuba, lallai kun cika marasa tsoron Allah, me kuma Imaan xata yi da kai ko Mujaheed Idan ba sa6o kake son yi ba, ka ja mana fushin ubangiji...." Murmushi kawai Yusuf yake, imaan ta nufi kofa xata fita, still tayi jin kamshin Mujaheed, juyawa tayi da sauri ta nufi dakin inna tana cewa "Kar ku ce masa ina nan" Mujaheed ya shigo parlon bayan few seconds, inna ta xauna tace "Imaan dai bata nan idan ma ita ka xo nema" Mikewa Yusuf yyi ya nufi kofa ya fita. Bedroom dinta Mujaheed ya nufa direct, inna tace "Da dai ka kinkimota ku fito don na share dakina tasss ba ko kwayar datti, kada a bata min a cuce ni ba uban wani ke min gyaran ba" Imaan na jin dama inna tace masa bata nan tasan dole xai shigo dakin, ta shige bayi da sauri ta sa makulli, Mujaheed ya murda kofar bathroom ya ji a kulle, juyawa yyi ya dawo parlor yana kallon inna yace "Kiyi mata magana ta ban wayata kada in sa ta kuka" Inna tace "Ikon Allah ya fi gaban haka, lkcn da wayar ya fita hannun ka ya shiga nata sani nayi Mujaheed? Kaji min raini dai, ni dai ta fito min daki gaskiya don ba Aisha bace ta share min" ya gyada kai ya juya ya fita parlon, Da kyar Imaan ta yarda ta fito bayan tafiyarsa da kusan minti goma, Inna dake tsaye bakin kofar bathroom din tace "To uwar me kike masa da wayar sa ya taba ki ya taba alakakai ya taba jaraba, ke dai ki daina tsokanan mutane kiyi ma kanki fada Imaan" Imaan ta fice a dakin, inna tace "Da dai ya kama ki ya nakada maki shegen duka da xai gigitaki in ga me ce masa don me a gidan nan, yarinya kawai kamar yar aljanu, wannan iri ta Bukar Allah ka raba mu da ita lafiya, duk da dai lkci ya kusa" A hankali Imaan ta bude kofar parlorn inna ta fita, ta gwammace tayi xagaye da ta bi normal route, da gudu ta shige parlon su ta sa makulli tana murmushi. Karfe tara da wani abu Ammi ta shigo dakin Imaan, Imaan dake xaune gaban madubi ta fito wanka kenan tace "Na xaton fa kinyi bacci" Ammi tace "Ki ji da ni kwanciya xan je inyi" mikewa tayi ta hau saman gado Ammi na kallon wayar kan gadon tace "Wayar waye wannan?" Imaan tace "Na yaya ne" Ammi na mata wani kallo tace "Me wayarsa yake a nan?" Kamar xata yi kuka tace "Ammi to ya dauke min nawa wayar ya ki ya bani" Ammi na kallonta da kyau tace "Kin san Allah idan baki kame kanki gidan nan ba kin raba kanki da Mujaheed sai na sa6a maki Imaan, yaushe ke da shi ku ka fara shirin da har xa ki dauke masa waya?" Imaan dai bata ce komai ba, Ammi ta hade rai sosai tace "Let me make it brief, daga yau na datse sabon alakar ku na gulma da Mujaheed, duk kika kuskura naga sabanin abinda nace wllh sai kin sha mamaki na, ko dama kin hada wani abu da shi ne ban sani ba? Kuma maxa ki kai ma inna wayar ta basa kayansa, naki kuma idan ya ga daman baki toh, idan kuma bai baki ba ki bar sa, hope am clear?" Kai kawai Imaan ta daga mata a hankali, Ammi tace "Shegantaka kawai, wai wani yaya, A'a ba yaya ba yayo, in sake ganin kin kalli inda yake a gidan nan idan ban tsole maki idanuwa ba" daga haka ta shafa mata lotion din maganinta sannan tace "Ki rage fan din, sai da safe" daga haka Ammi ta fita ta kulle mata kofa, Imaan ta saka kayan baccinta ta koma mirror tana shafa lotion a kafarta taji ana bude window, mikewa tayi da sauri tana kallon window din, ido hudu suka yi da Mujaheed ta dauke kai, strictly taji yace "Bani wayata" Ta make kafada tace "Nima ka bani nawa first" Yace "Na fara maki wasa a gidan nan koh?" Ta ki cewa komai ta daura kafarta kan stool dake gaban mirror tana shafa lotion dinta, jin shiru ta juya, kallonta taga yana yi da lumsassun idanuwansa, ta hade rai tace "Yaya yanxu idan sauro ya cije ni na fara rashin lafiya fa? Dubi yanda ka bude min window fa, ni dai ba ruwana idan na fara ciwo" calmly yace "Kar ki bari in shigo gidan nan, wllh xan sa ki kuka, give me my phone I want to use it" yar dariya tayi ta dau turare tana fesawa, yace "OK kina xaton baxan iya shigowa bane?" Ta wara ido tace "Toh ai bance maka kar ka shigo ba" Tana fadin haka ta karasa saman gado ta kwanta ta rufe da duvet, rufe window din yyi yana gyada kai ya bar wajen. Mujaheed xai shiga parlon su suka hadu da Daddy, gaida sa yyi da ladabi daddy na tambayarsa ya aiki yace "Alhmdllh" yana tsaye har daddy ya shiga gun Abba, ya d'an yi jim, can ya tafi apartment din su imaan, ya fi second goma tsaye ya kasa bude kofar, A hankali ya murda kofar ya shiga yana kallon cikin parlon, babu kowa sai tv dake kunne, dakin Imaan ya nufa ya bude kofar, kwance ya ganta har ta yi bacci, ya dinga bin dakin da kallo ya karasa kusa da ita, daukar wayarsa da ta ajiye bedside drawer yyi yana kallonta, gaba daya ta takure waje daya saman gadon sleeping peacefully sai dai ta cire duvet din, dauka yyi ya rufa mata ya tafi gun switch din fan din dakin ya kashe fan din gaba daya ya juya xai fita yaga Ammi tsaye bakin kofa, still yyi ya kasa cewa komai, lkci daya ya sauke kansa ya fara kame kame yace "I... I came to take my phone" *The book Imaan is not free, you read for free ur cup of coffee*🤷🏻‍♀️ It's 300 via Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah Then u show ur evidence of payment via my WhatsApp digit 07087865788 to be included in the payment group. Ammi ta dinga kallonsa kafin a nutse tace "I want to give u this warning Mujaheed, stay away from Imaan" shi dai bai yarda ya kalleta ba, bai kuma ce komai ba, juyawa tayi ta bar bakin kofar, Mujaheed ya fita xuwa kofar fita parlon. Washegari da safe Imaan ba inda bata duba ba a dakin tana neman wayar Mujaheed ganin bata gansa inda ta ajiye ba, kamar xata yi kuka ta fito parlor sanye da uniform din islamiyya, tana kallon Ammi a hankali tace "Ammi kin ga wayar nan na jiya?" Ammi ta mata wani kallo tace "Wanda kika bani ajiya?" Shiru tayi bata ce komai ba, Ganin ko kallonta Ammi bata sake yi ba ta juya ta wuce dinning don yin breakfast, mamaki ta dinga yi ta ya xata nemi wayar ta rasa a inda ta ajiye, daga karshe tayi concluding kawai Ammi ce ta boye, ta tura soyayyen dankalin gabanta ta mike ta dawo cikin parlor, safarta ta sa ta xura Hijab din makarantarta ta dau jaka tana kallon Ammi dake parlor kamar xata yi kuka tace "Ammi fa kila xai yi amfani da wayarsa don Allah ki bani in kai masa plss" Ammi ta daga kai tana kallonta, da sauri Imaan ta fice daga parlon don ta san sauran, parking space ta tafi ta tsaya tana jiran su Maimoon su fito, Mujaheed ne ya fito tare da Yusuf, Imaan ta dinga kallon hannunsa da mamaki ganin wayarsa, bai ko kalli inda take ba ya nufi gun motarsa ya bude ya shiga, Yusuf dake kallonta yyi murmushi yace "Why are you looking at him that way" kamar xata yi kuka tace "Ya Yusuf jiya ya dauke min wayata shine nima naje dakinsa na dauke nasa toh yanxu ga na sa a hannunsa ban san ya aka yi ya dauke ba, ni kuma nawa har yanxu ya ki bani" Yusuf yace "Toh me yasa ya dauke wayar ta ki?" Tace "Nima ban sani ba kuma har daki na ya shiga ya dauka, ni dai wllh ya bani waya ta xan je in gaya sa da inna" Yusuf ya kalli Mujaheed da har ya tada motarsa amma idonsa na kansu, dauke kai Yusuf yyi yace "Yaushe har ku ka fara shiri da Mujaheed da har ya shiga dakin ki ya dauke waya?" Ta turo baki tace "Ni ba wani shirin da mu ke, kawai ganinsa nayi a dakina bayan Ammi da daddy sun fita" Yusuf ya sake kallon Mujaheed da yaki driving din motarsa, ya dauke kai, Imaan tace "Ya Yusuf ka yi masa magana plss kuma fa ana kirana a wayar" Yusuf yace "Wa ke kiran ki?" Boye fuskarta tayi ta fara dariya, Yusuf ya dinga kallonta, ta xame Hijab din da ta rufe fuskarta a hankali, sai a sannan ya sauke idonsa yace "Baxa ki gaya min ba" ta wara ido tace "Ya Yusuf wani ne, he is my friend" jin Yusuf bai ce komai ba tace "Ni dai kafin su fito bari in je in gaya ma inna" daga haka ta wuce ya bi ta da ido kamar yanda Mujaheed ma ya bi ta da kallo, waje ta ga inna tana ta faman goge window with seriousness, Imaan tace "Ina kwana inna" Inna ta d'an kalleta kafin ta dauke kai tace "Aa ba wani inna ina kwana, ke din ce xa ki xo gaisheni takanas da safe, ke dai fadi abinda ya kawo ki ina ji" Imaan tace "Toh ko ba yaya bane ya dauke min wayata tun jiya ya ki bani" Kamar xata yi kuka ta kare maganar, Inna ta ajiye tsumman hannunta a bokiti da mamaki tace "Waye kuma yaya?" Imaan ta rungume hannunta xata yi kuka, inna tace "Lallai ba lafiya, shi Mujaheed din akwai wani alaka ne tsakanin ku wanda ni ban sani ba da har xai dauke maki waya? ko sata ya fara yi ba a sani ba a gidan, ni dai naga abinda ya isheni, gaskiya wannan d'a na Ahmadu yana cutar mu a gidan nan, to meye kuma xai dauke maki waya kamar shi ya siya? ko yana bin ki bashi ne? Toh a gaskiya ya kamata Mujaheed yyi aure ya kama gabansa na gaji da maganarsa kuma haka Allah ya gani nayi kokari, shekara kusan talatin da biyu ana abu daya, wannan ai fitinanne ne mara son xaman lafiya, mu je gun Ahmadu in ji ko shi ke koya masa ya dinga walakanta ni a gidan nan" daga haka inna tayi gaba imaan ta bi bayanta, Inna ta tsaya kamar warce taga mugun abu ta juyo da sauri tana kallon Imaan tace "Toh da ya dauke wayar ta ina Bulasawan ke kiran ki?" Imaan tace "Toh ba wayar na wajensa ba, kila ma ana ta kirana ya daga" Inna ta saki salati tace "Ashe yau xa a ga barbadin fitina a gidan nan, mu je gun Ahmadun" Yusuf na nan tsaye inda yake, Mujaheed kuma ya wuce kenan inna ta iso kamar xata tashi sama, Yusuf na kallonta yace "Ina kwana Inna" a fusace ta juya tana kallonsa tace "Da ban kwana ba xaka gan ni, ko a titi kake gaida uwarka Amina, to hirr dinka... Dama duk gantalallen da yace jikata xai sa ma ido ya dinga yi ma bakin ciki to yyi ta kansa inyi nawa a gidan nan, ba ruwana, kada ma ka sake gaisheni bana so, ko kuma in tsine ma gaisuwar...." Kallonta kawai Yusuf yake bai ce komai ba, Inna ta wuce kamar xata tashi sama, imaan da ta ki yarda ta kallesa ta bi bayanta, Anty na goge goge parlon Abba inna ta shiga imaan na biye da ita, Anty tana kallonta tace "Ina kwana Inna?" Inna tace "Ke ba xancen ina kwana, Amina ashe kema jaraban kika haifa ban sani ba sai jiya, ashe Isuhu ma ba mutumin kirki bane na banxa ne ni ban sani ba, ashe halinsa daya da tijararren nan Mujaheed, to Ahmadu ya ga ta kansa kuwa don wannan ba yaran nunawa bane, banda haka ta ya xa su nuna bakin ciki da hassadansu a fili kan jikata, daga Allah ya axurtata da mai kudi saurayi sabon jini sai hassada ya tashi? toh wllh su cire idanuwansu kan imaan, shi Isuhu tsabar shaharan da yayi a fannin bak'in ciki ce min yyi a bar xancen sabon saurayin ma gaba daya, ke ki ji min mugunta, kice min lalacewa bai xo duniya ba?? saboda mamakin abinda yace min sai nake tambayarsa ko idan aka bar batun sabon saurayin su xa su aureta?? Budan bakin katon sai ce min yyi to na sani ko su xa su auretan? Ke ki ji wani sa6o fa, kawai ya ja gida ya rushe da ni a ciki" Inna ta fara matsar kwalla tace "Yanxu Isuhu bai ji kunyar gaya min haka ba, idan ba ta6ewar basira ba dama ina su ina Imaan daga shi har Mujaheed din, wllh ta fi karfinsu, me garesu da har xa su rike min ita salon wataran in xo daukar gawarta ina kuka suna bani hakuri, haka kawai su kai ni su baro, yanxu fisabilillahi Allah ya dubeni ya fiddo mata dai dai ita kuma sai bakin cikin yan uwa ya tashi, to Allah ya so ni dama ba abinda na hada da su, ba dangin iya balle na baba, kawai ni dai nasan na haifi Ahmadu shi kuma ya haifesu, ni sai ince Bukar ya tattara ya bar gidan ma...." Shigowar Abba yasa ta dakata, Abba na kallonta yace "Lafiya inna?" A fusace tace "Ina fa lafiya Ahmadu isuhu da Mujaheed sun fi karfina, kawai yaro ya dage ya kwace ma yarinya waya sai kace Rukayya ce ta siya wayar, to wllh kafata kafar wayar nan yau idan ba haka ba in bar kowa da Allah, kuma gaskiya a daina bata min rai gidan nan don duk ranan da xuciya ta debeni idan ban bi Bukar Abuja ba ace bani bace" Abba dai ya kasa cewa komai, Ajiyar xuciya Anty ta sauke tace "Toh ina Mujaheed din?" Inna tace "Sai ki tambayeni Mujaheed ba tare ku ka kwana gidan nan ba ke kuma" Abba ya dau wayarsa yyi dialing number Mujaheed, Mujaheed na driving ya daga wayar, Abba yace "Where did you drop imaan's phone?" A hankali Mujaheed yace "It's with me" Abba yace "Bring it back now" daga haka Abba ya katse wayar, inna ta xauna kan kujera tana kallon Imaan tace "Xauna mu ga ta inda wayar xai fito" Imaan da ta ki yarda ta kalli Abba ko Aunty ta karasa kusa da inna ta xauna, Inna tace "Ahmadu dai bai yi sa'an 'ya ya ba gaskiya, don Mujaheed da Isuhu sai su iya kashe mutum" Anty ta ci gaba da aikin da take yi, Inna sai girgixa kafa take bayan kusan minti goma sai ga Mujaheed ya shigo parlon, Inna tace "Huuuu an dai ji kunya, fito da wayar da ka dauke" Mujaheed dai bai ko kalleta ba ya mika ma Abba wayar, Abba ya mike ya ba inna, inna ta karbe ta mika ma imaan tace "Tashi mu je, daga yau dama duk inda kika ga Mujaheed ki canza hanya da gudu don ba mutumin kirki bane" Imaan ta mike ta bi bayan inna, inna ta bude kofa tana cewa "Sai kuma ka sace wayar Rukayya idan ta ajiye ba dai na imaan" Karfe biyar saura na yamma Sadeeq yayi parking kofar gidan su Imaan ya kashe motarsa ya jinginar da kujeran motar, Muhsin dake kallonsa yace "Ya da gyara xama kuma Doctor" Sadeeq ya shafa kansa a hankali yace "Ni fa I told you ban taba xuwa gidansu yarinyar da nake nema gun iyayenta ba, I don't even know where to start from, to idan ma na shiga me xan ce masu? All that aside, ni ban ma san me yasa ake nemana ba" Muhsin yyi dariya yace "Toh dama kuwa ina xaka je gidan su yarinyar da kake nema bayan duk turawa ne Sadeeq, kaga kawai idan baxa ka iya shiga ba mu rabu da su mu koma kada mu je ka kunyata ni gaskiya" Sadeeq ya sauke glass din idonsa yana kallon Muhsin, can yyi murmushin sa mai kyau cikin cool voice dinsa yace "In koma fa kace" Bai jira cewar Muhsin ba ya mayar da glass dinsa ya bude motar ya fita, sanye yake da kananun kaya da suka yi matukar amsan jikinsa, Muhsin ya fito motar yana kallonsa yace "Ehh lallai Abokina ya xurma da yawa" Sadeeq dai bai tanka sa ba ya gama danne danne wayarsa ya kai kunne, bayan wani lkci yyi kasa da murya yace "Abba gani a waje" Abba dake xaune parlonsa tare da Daddy yace "To madallah bari they will lead you in now" Ba a dau lkci ba Yusuf ya fito kofar gidan, Kallon Sadeeq ya dinga yi har ya isa inda suke, suka gaisa Muhsin yace "Ashe dai Engnr kana gari?" Yusuf yyi murmushi yace "Sure ina nan, ya aiki" Muhsin yace "Alhmdllh" Yusuf ya shiga da su compound din har xuwa parlon Abba, Sadeeq na shiga parlon ya cire glass yyi kasa da kai har xai xauna saman kujera sai kuma ya fasa ya xauna kasan rug ganin nan Muhsin ma ya xauna, har sannan bai dago kansa ba ya gaida su Abba da Daddy, duk suka amsa suna masa sannu da xuwa, Daddy yace "Muhsin abokin ka ne dama kenan" Muhsin yace "Ehh Abba abokina ne" Daddy ya gyada kai yace "That's good" Abba ya kalli Yusuf da ya xauna yace "Where is M.A?" Bude kofar parlon aka yi sai ga Mujaheed ya shigo parlon da sallama can ciki, kansa a kasa ya xauna kusa da Yusuf sannan ya kalli Sadeeq da idanuwansa ke kan TV, gaisawa yayi da Muhsin, sai a sannan Sadeeq ya kallesa yace "Barka da yamma" Mujaheed yace "Same to you" Abba na kallon Sadeeq yace "Can I know you plss son" Sadeeq ya sauke idonsa kasa yace "Sunana Abubakar Sadeeq Ahmad, ni haifaffen garin Kaduna ne, mahaifina asalinsa d'an kano ne, na gama karatu na and I am working as a medical practitioner now" Abba yace "Maa sha Allah, a wani anguwar ku ke?" Yace "GRA muke" Abba yace "Ohk can i know ur dad?" Sadeeq ya d'an yi Shiru kafin yace "Alhaji Ahmad sunansa, d'an kasuwa ne Abbana, yana kuma xaune nan Kaduna" Abba ya gyada kai cike da gamsuwa, bayan few seconds yace "What is ur intention toward my daughter Abubakar?" Sadeeq ya kasa dago kansa, Daga Mujaheed har Yusuf kallonsa kawai suke, can ya dago kansa a hankali yace "Abba sonta nake da aure...." Mikewa Yusuf yyi yana kallon Abban nasa yace "I want to excuse my self plss..." Abba ya gyada masa kai ya juya ya fita parlon, Abba yace "Toh naji dadin jin hakan daga gare ka Abubakar amma kasan ajin da Imaan take yanxu?" Ya gyada kai a hankali yace "Na sani Abba" Abba yace "Ohk good, wani xancen kuka yi da kakarta last time da ka xo?" Murmushi yyi ya sunkuyar da kansa, Abba yace "Yes go on" Yace "Abba ce min tayi idan tayi magana da ku xata sanar min in turo magabatana" Abba yace "Ohk, kai d'an wajen Ahmad Bulasawa ne?" Sadeeq ya gyada kai kawai, Abba yace "To yayi kyau, yanxu dai I want to ask for a favor from you Sadeeq" Sadeeq ya daga kai a hankali yana kallonsa, Abba yace "But before then bari in maka wannan alkawarin, Sadeeq in dai Imaan ta amince tana son aurenka, wato ta yarda da kai, sannan iya binciken da xanyi idan ban ga wani flaws dinka mara kyau ba ni nayi maka alkawarin xan baka Imaan in sha Allah, yea it's a promise I am making" mikewa Mujaheed yyi yana kallon Abba yace "Abba I want to pick a call" bai jira cewar Abba ba ya fita, Sadeeq dake kallon Abba yace "Toh nagode Abba" Abba yace "Toh favor da nake son ka min ynxu shine.... Kakarta nake son ka samu amma ba yau ba, but cikin satin nan, sai ka ce mata mahaifin ka bai kasar yanxu kuma xai dau lkci kafin ya dawo, yana dawowa kuwa xaka sanar masa xancen auren... Am doing this to allow my daughter finish her secondary schl, wato na da shekara daya, kasan yanda tsoffin nan suke, there is nothing da xan gaya mata da xata fahimce ni, amma kai idan kace mata haka to an gama komai, kaga ko da tana gamawa ne sai ayi magana amma yanxu kam I don't think xan iya bada ta tana ss2, that aside.... my promise of giving u my daughter's hand in marriage will count only on one condition ko da ta gama secondary schl, the condition is that xaka yarda ko bayan kun yi aure ta ci gaba da karatu a dakinta" Sadeeq ya d'an yi murmushi yace "In sha Allah Abba" Abba yace "Toh Allah ya mana xabi mafi alkhairi" Sadeeq yace "Ameen Abba na gode sosai, Allah ya kara girma" Abba yace "Allah maka albarka" daga haka Abba yace masa xai iya tafiya, nan suka yi sallama da Daddy da Abban sannan suka fita parlon. Muhsin na kallonsa yace "Mu je in gaida Mum dita" Sadeeq ya xaro ido yace "No kai dai kaje zan jira ka a waje" Muhsin yyi dariya yace "Common Mum dita fa na ce maka..." Da kyar ya ja Sadeeq suka nufi part din su imaan, Bell Muhsin ya danna, Ammi na kitchen xata fito Imaan ta bude kofar dakin ta, Wani kallo Ammi tayi mata tace "Kika san waye bakin kofar xa ki tafi a haka?" Imaan ta xaro ido ta juya ta koma ta dau Hijab dinta ta sa ta fito ta nufi kofar, bude kofar tayi, lkci daya tayi still tana kallon Sadeeq, Muhsin yace "Toh ko mu bi ta kanki" da sauri ta juya ta bar wajen, kafin su shiga parlon har ta koma dakin ta ta kulle, Dariya Muhsin yyi ya xauna, Sadeeq that was uncomfortable shi ma ya xauna, Ammi ta fito kitchen ganin Muhsin tace "Ka shigo anguwar kenan" yayi dariya yace "Ammi takanas nan fa na xo wllh" tace "Keep quiet kai din" yace "Ki tambayi abokina Ammi" Ammi ta karasa shiga cikin parlon tana murmushi tace "Toh sannun ku da xuwa" Muhsin ya gaidata, tun da Sadeeq ya kalleta sau daya bai sake yarda ya kalleta ba shi ma ya gaisheta, ta amsa da fara'a tana masu sannu da xuwa, Muhsin yace "Kawai ce masa nayi ya rakani in gaida Mum dita" Ammi tace "Toh kun kyauta kuwa nagode, sai dai abokin naka kamar d'an uwan mu ne Bafillatani" Dariya kawai Muhsin yake, Sadeeq dai yyi murmushi bai dago ba, Ammi ta tambayi Muhsin yayanta sannan ta tambayi Sadeeq iyayensa, Sadeeq yace "Duk suna lafiya lau" Ammi na kallon kofar dakin Imaan tace "Imaan" Muhsin yace "Kawai daga gani na shine ta shige daki saboda bata da gaskiya bata gaida mutane ko a waya" Dariya Ammi tayi tace "Ae ban san yanda xanyi da ita ba, ko nace tayi sai tace ta manta" Sai da Ammi ta kara kiranta ta fito da kyar, wannan karan Hijab har kasa ta sa, Ammi tace "Baxa ki gaida yayanki ba kika shige daki?" Bata yarda ta daga kanta ba har ta iso cikin parlon kamar munafuka ta xauna kasa kusa da kujera tace "Ina yini Ya Muhsin?" Yana murmushi yace "Lafiya lau Imaan, ya gida?" Tace "Lafiya lau" ta saci kallon sadeeq da yaki kallon inda take tace "Ina yini" yace "Lafiya lau" Ammi tace "Ki dauko masu ruwa fridge" mikewa tayi ta wuce kitchen, Ammi tace "Jiya mun yi waya da yaya yace gobe xai dawo" Muhsin yace "In sha Allah, haka yace min" Imaan ta shigo cikin parlon ta durkusa ta ajiye tray din ruwa da lemon five alive sai glass cups biyu, Ammi tace "Na gama girki bari in xubo maku" Muhsin yace "A'a ki bar shi kawai Ammi a koshe mu ke..." Ammi tace "Idan kai baxa ka ci ba sai abokin naka ya ci, ya sunansa ma dai?" Dariya Muhsin yyi yace "Sunan Daddy garesa" Ammi tayi murmushi tace "Ikon Allah, mai gida ne ashe" Muhsin ya kasa daina dariya, Imaan na ajiye drinks din dama ta shige daki ta kulle kofa, Ammi na shiga kitchen Sadeeq yyi kasa da murya yace "Don Allah ka rufa min asiri mu wuce Muhsin" ko kallonsa Muhsin bai yi ba ya mike ya bi bayan Ammi kitchen, har ta fara xuba masu abincin a plate yace "Ammi kinsan waye muke tare da kuwa?" Ammi ta juya tana kallonsa tace "A'a, waye?" Kasa daina dariya yyi yace "Wllh surkin ki ne, saurayin Imaan" Ammi ta saki serving spoon din hannunta tana kallon Muhsin baki sake tace "Amma baka da kirki Muhsin shine ka bar ni ina ta xuba a parlor?" Dariya kawai Muhsin yake, Ammi tace "Ni dai ba ka kyauta min ba, haba naga yaro ya ki sakin jiki, ita kuma Imaan sai na ci mutuncin ta..." Da sauri ya dakatar da ita yace "Wllh bata sani ba, baki ga ita ma duk ta ki sakin jiki ba" Ammi tace "Ni dai ka cuce ni, har kasa naje ina ce masa mai gida" Shi dai bai fasa mata dariya ba, ta gama xuba abincin tace "Ai sai ka daukar maku, ni kam na wuce daki" bata kara sauraransa ba ta fita kitchen din ta wuce bedroom dinta, Muhsin ya ci abincinsa ya koshi, Sadeeq kam ruwa kawai ya sha ya mike yace "I am waiting for you outside" duk yanda Muhsin ya so tsayar da shi kin saurarensa yayi har ya fita, nan Muhsin ya kira Ammi a waya yace "Toh ya dai fita Ammi ki fito mu yi sallama" Ammi ta fito parlon tace "Bai ci abincin ba kenan" Muhsin yace "Ae baxai ci ba, Ammi Abbansu Mujaheed ne fa ya kirasa yana nemansa shine muka taho tare" Ammi tayi shiru tana kallonsa da mamaki, can tace "Toh ya aka yi da ku ka je?" Muhsin yace "Ba wani matsala wllh, Ai nasan daddy xai maki bayanin komai idan ya shigo, yanxu dai xan wuce kinga yana can waje yana jirana" Ammi tace "Toh shikenan ka gaida Hajiya da Hajjo" Yace "In sha, kice ma Imaan ta fito mu dai mun wuce" daga haka ya fita parlon yana murmushi, a can kofar gida ya tadda Sadeeq xaune cikin mota yana jiransa, Muhsin ya bude motar ya shiga yana kallonsa yace "Kai dai ka rage munafurci Sadeeq duk rashin jin ka don ka xo gaban surkai sai kayi ta wani sinne kai" Murmushi kawai Sadeeq yyi ya saka glasses dinsa ya tada motar yace "I will have ur time later" daga haka ya fara reverse suka bar layin. Kamar yanda Muhsin ya fada hakan ne ya faru don daddy na shigowa bayan Magrib ya yi ma Ammi bayanin duk abinda ke faruwa, Ammi tayi shiru duk jikinta yyi sanyi, A hankali tace "Toh yanxu ya ake ciki yallabai?" Ya sauke ajiyar xuciya yace "Ina imaan din, taje can barrister na kiran ta" Ammi tace "Ni dai Yallabai da dai a dakatar da yaron gaba daya, imaan har nawa take don Allah" Daddy yace "So kike ki ja mana matsala gun inna kenan, did you know maganar da ya dawo dani weekend kenan, ke kin ga abubuwan da inna ta dinga fadi a parlor kuwa jiya?" Ammi dai bata ce komai ba, Daddy ya girgixa kai yace "Fatanmu mu rabu da ita lafiya, gaba daya ta rikice ne yanxu" murmushi kawai Ammi tayi, Daddy yace "I don't even know me yasa xa ki ba Imaan fuskar kula saurayi at the first place, ko me xaki ce min baxan ta6a yarda baki san da xancen yaron ba, kuma ki wani ce min nawa Imaan take?" Ammi tace "A'a ko da baxa ka yrda ba I have to tell you I know nothing much about the boy, of recent naga tana waya shi ma sai da na mata fada, kai sai kace baka san yar taka bace da nuku nuku" Daddy yace "Wannan ba hujja bace, kina tare da ita 24/7 a gida...." Ammi ta dakatar da shi tace "Toh duk ba wannan ba ita innar da ta kirkiro abun sai a fada mata ta gaya ma yaron lalurorinta... If he wish to be with her like that shikenan, idan kuma baxai iya ba gwara tun wuri a san haka, I don't want my daughter's heart to be broken or anything of such..." Daddy ya dinga mata wani kallo ta mike ta wuce kitchen, yace "Wato you are even in support of the silly thing the girl did, dama nasan kinsan komai ai, tunda aure take so fine I will give her the best wedding ever" Imaan ta marairaice tana kallon Ammi tace "Toh me yasa yake kirana Ammi?" Ammi tayi banxa da ita, a hankali ta mike ta nufi kofa, Ammi tace "Kuma kiyi maxa ki dawo idan ya sallameki ki xo ki kai ma Inna abinci" to kawai tace ta fita parlon. A hankali Imaan ta bude kofar parlorn hade da sallama ta shiga ciki, Umma ce xaune parlor sai Ummi da Rahma, ta dauke xata wuce parlon Abba Umma ta dakatar da ita ta hanyar daka mata tsawa, Imaan ta tsaya amma bata juyo ba, Umma ta mike tana mata kallon tsana karara tace "Uwarki tayi ajiya parlon ne ta aiko ki kixo ki dauka?" Imaan taki cewa komai sai ma dauke kanta da tayi, Xagi Umma ta kunduma mata tace "Kin matsa bakin kofar nan ko sai na faffalleki da mari"Imaan dai bata tanka ta ba ta nufi stairs, Umma tace "Ragowar ciwo kawai" Sai da Imaan ta isa stairs ta turo baki ta wuce sama, sai kuma ta fashe da kuka, dai dai corridor suka hadu da Mujaheed ya fito dakinsa, ya bi ta da ido har ta shiga dakin Aunty, Karasawa stairs yyi yana lekan downstairs ganin Umma xaune ya dawo da sauri ya bude kofar dakin Aunty ya shiga ya kulle, Aunty na tsaye kanta sai tambayarta me ya faru take hankali tashe, Imaan da ta xube mata nan tsakar dakin ta dinga kuka ta ki cewa komai, Aunty tace "Kinga iskancin nan naki ne bana so, baxa ki bude baki ki min magana ba, me kika yi ma Ammin?" Still ta ki cewa komai, Mujaheed ya karasa kusa da su yana kallonta yace "Baxa ki bude baki ba ana maki magana?" Ta hade kai da gwiwa cikin rawar murya tace "Ko ba Umma bace take xagina ni ban mata komai ba har da ce min ragowar ciwo" Aunty ta ja tsaki tace "Shine xaki xo ki tada min hankali a nan? Sai me don ta ce maki ragowar ciwo? Xa kuwa ta ga ragowar ciwo a xuri'arta wataran, domin ita ta gama haihuwa ai yanxu su kuma 'ya yanta xa su fara...." Juyawa Mujaheed yyi ya nufi kofa, Aunty ta bi sa da harara har ya fita, Aunty tace "Banda shashanci shine xaki xo kina ma mutane kuka, yau ta saba gaya maki haka?" Ita dai Imaan bata ce komai ba sai share idonta take, Anty tace "Aiko ki Ammi tayi ko me?" Ta dago ta kalleta a hankali tace "Abba ne ke kirana" Aunty tace "Tashi mu je, yana parlon sa ai" mikewa imaan tayi ta bi bayan Aunty suka fita, Umma ta dinga bin su da wani kallo, Aunty ta nufi parlon Abba tana cewa "Ae ba mahalukin da ya isa raba ki da ubanki, sai dai a ganki a kyale bbu ynda aka iya da ke" Aunty ta bude mata kofar tace "Shiga" Imaan ta shiga parlon Aunty ta rufe kofar ta koma sama, Abba na xaune yana kallon news Mujaheed ma na parlon, sallama Imaan tayi ta xauna kasa ta gaida Abba dake kallonta, yace "Lafiya lau Mamana sai yanxu kika xo?" Kai kawai ta gyada masa, Abba yace "Toh yayi" bai kuma cewa komai ba, Imaan ta saci kallon Mujaheed taga kallonta yake, suna hada ido ya hade rai, turo baki tayi tana fidgeting fingers dinta, Bayan few minutes Abba yace "Imaan ai kin san wannan yaron Sadeeq koh?" Shiru tayi bata ce komai ba ta kuma kasa kallon Abba, Abba yace "Ina saurarenki" ta gyada masa kai tace "Uhm" Abba yace "Kar fa ki boye min komai I am ur father, ki gaya min meye tsakaninku" dauke kai tayi ta ki cewa komai, Abba yyi murmushi yace "Baxa ki gaya min ba kenan" Nan ma dai ta ki cewa komai, Abba yace "Toh tunda ni kunyata kike ji sai ki gaya ma Mujaheed meye tsakanin ku" Xaro ido tayi tana kallon Abba, Abba ya mike yace "Xan dawo yanxu, let me make a call outside, sai ki gaya masa kafin in dawo shi kuma ya gaya min" daga haka Abba ya fita ya kulle kofar, tun da Abba ya fito Umma ke binsa da kallo har ya fita main parlor, ta kalli kofar parlon sa.... Imaan dai ta kasa xaune waje daya bayan fitar Abba, jin shiru ta d'an saci kallon Mujaheed, ganin irin kallon da yake mata xata mike yace "Koma ki xauna" ta marairaice tana dubansa tace "Ni fa ruwa xan je in sha in dawo" ya dawo kusa da ita ya xauna yana kallonta da kyau cikin husky voice dinsa yace "Me nace ki ce ma Abba?" Ta 6ata fuska kamar xata yi kuka a hankali tace "Yaya ba ka riga ka gaya min jiya ba, ai xan gaya masa...." Sai kuma tayi shiru, ya hade girar sama da ta kasa yace "I will slap you idan baki gaya min abinda xaki gaya masa ba" Tace "To ba cewa kayi ince ban san sa ba...." ya dinga kallonta fuskarsa daure, a hankali ta mike da nufin fita parlon ya fixgota ta fado jikinsa, xaro ido tayi tace "Yayaa" bude kofar parlorn aka yi yyi saurin janyeta jikinsa, Kallonsu Aunty ta dinga yi daga inda take tsaye bakin kofa, Mujaheed duk ya daburce ya mike tsaye, Imaan ta zamo kasan kujeran kamar xata yi kuka, Aunty tace "Meye hakan" Mujaheed yace "Aunty kawai daga mata magana shine xata fado kaina" Aunty ta tabe baki har sannan tana kallonsu, juyawa tayi xata fita sai ga Abba, ta basa hanya ya shigo parlon, Anty ta fita waje, Abba na kallon Mujaheed bayan ya xauna yace "what did she say about him?" Mujaheed ya xauna saman kujera yana shafa kansa a hankali yace "Tace ba komai tsakaninsu, bata ma wani sansa ba kawai shine ke kiranta a waya..." Imaan ta kallesa da sauri, Abba yace "Haka ne Imaan?" Kamar xata yi kuka tace "Abba ni dai bance masa haka ba, frnd dina ne fa, kuma yana koya min karatu ta waya wani lkcn, ina ganewa kuma" Mujaheed ya kasa kallon Abbansa, Abba ya kafe sa da ido, can ya d'an yi murmushi mara sauti yace "Toh shikenan mamana, tashi ki tafi" mikewa tayi ta nufi kofa, xata fita ta d'an saci kallon Mujaheed da ya ki dago kansa ta fita. Bata damu da irin kallon da Umma ke mata ba har ta fita parlon ta wuce part din su. Abincin inna ta dauka ta tafi kai mata, sallah ta sameta tana yi a parlor ta ajiye abincin xata fita, inna ta dinga gyaran murya alamar ta tsaya, imaan tayi kamar bata ji ba tayi wucewarta da sauri, a hanya ta tadda Yusuf rike da ledan fruits xae kai ma inna, ta gaishesa tana kallonsa, sama sama ya amsa mata ya wuce, ta tsaya ta bu sa da kallo har yyi nisa, turo baki tayi ta bar wajen, har ta gama shirin kwanciya kiran Sadeeq ya shigo wayar ta, ta kashe fitilan dakin ta hau saman gado ta rufe har kanta da duvet sannan ta daga kiran, murya can kasa ta amsa sallamansa yace "Kin fara bacci ne?" Ta girgixa masa kai tace "A'a" murmushi yyi yace "Toh ya kike?" Tace "Alhmdllh, ya aiki?" Yace "Lafiya lau..." A hankali tace "Shine daxu baka ce min xa ku xo da ya Muhsin ba koh?" yyi murmushi yace "Shi yace kar in gaya maki" tace "Toh yanxu da kun sameni ban sa Hijab ba fa?" Ya wara ido yace "Yea sai in ganki da kyau, ai ba laifi bane don naga abinda nake so ba hijab" ta xaro ido tace "Uhnnn?" Yace "Yess" murmushi tayi bata ce komai ba, Yace "Ya Ammi fa?" Tace "Tana lafiya" yace "Maa sha Allah, kinje gun kaka yau?" Tace "Ehh na je kai mata abinci" yace "Ina son in samu time in xo mu yi hira sosai da ke da kaka" ta xaro ido tace "Ai ita bata hira, bata fiye son magana ba ma" Dariya Sadeeq yyi yace "Really?" Kamar xata yi kuka tace "Ehh" yace "Uhm to shikenan, yaushe xan xo mu yi hiran mu biyu kadai, I want to tell you lot of things Imaan" Murmushi tayi tace "Ae Daddyna na gari bai koma ba tukun" Yace "Toh baxa ki gidan gwaggo ba mu hadu can?" Ta d'an yi shiru, murya can kasa yace "Are you there Imaan?" A hankali tace "Toh gobe xan ce ma Ammina xan je can dama ai saura kwana uku bikin Anty Halima kilan idan na je sai bayan bikin xan dawo gida" yace "Toh shikenan idan kin shirya goben sai ki kirani" ta xaro ido tace "But ai sai Ammi ta amince in je, kasan ba a son ina fita ni kadai" yace "Toh Allah yasa ta amince" Tace "Ameen" da sauri Imaan ta cire duvet din kanta jin kamar ana bude window, ganin farin abu tayi ya fadi kasan dakin, ta sauka gadon ta nufi windon da sauri ta bude labule har sannan waya na kare kunnenta, Mujaheed ne tsaye kusa da window din, ta xaro ido tana kallonsa, yana mata wani kallo ya juya ya bar wajen, ta rufe window din ta durkusa ta dau takardan tana kallo, muryar Sadeeq taji a kunnenta yace "Are you there?" Tace "Yea ina ji" yace "Ko kin fara jin bacci ne" murmushi tayi tace "Um" don so kawai take ta bude takardar ta ga content dinsa, yace "Toh shikenan, sleep like a baby dear" murmushi tayi tace "Toh nagode, good night" daga haka ta katse wayar ta ajiye ta kunna fitilar wayar ta warware takardan tana haska rubutun kai, xumburo baki tayi ta cukwuikuye takardan ta jefar ta kwanta kamar xata yi kuka tace "Ni dai ba ruwanka da ni" Mikewa tsaye Aunty tayi tana kallon Yusuf dake xaune gefen gadonta, shi kam bai yarda ya kalleta ba, Tace "What are you saying Yusuf?" Still ya ki cewa komai, aunty ta dinga kallonsa ko kiftawa babu, can ta ja stool ta xauna tace "Ka daga kai ka min magana malam" Sai a sannan ya daga kai ya kalleta, tace "Are you serious with what you are saying, or should i say are you on ur right senses?" Cikin sanyin murya yace "Sure Mum" Tagumi Aunty tayi tana kallonsa with much surprise, can ta girgixa kai cike da damuwa tace "Kai ma kasan wannan ba abu bane da xai yiwu, ba abu ne mai sauki, haba Yusuf me yasa ka yarda xuciyarka ta yaudare ka da son abinda kasan da wuya ka samu, ko da kuwa kana tunanin xaka samu mai yasa baka tsaya kayi naxarin irin matsalolin dake tattare da samun ba? Wait tukun toh ita Hafsat din fa?" Ya girgixa kai cikin low voice yace "Ku ke tunanin ina son Hafsat, she is just a frnd, bani da intention na auranta...." Aunty ta xaro ido tana kallonsa, can tace "Ikon Allah, i really don't know what to say to you now Yusuf, ban san me xance ba gaskiya, amma ni da xaka bi shawarata ka bar wannan xancen it's something that isn't and will neva be possible, forget this pls son" Yana kallonta da mamaki yace "Why Mum?" Tace "Look Yusuf, Imaan is my daughter, her mother is my very close frnd as well, infact childhood frnd dita ce Aisha, don ta dalilinta na hadu da mahaifin ku har muka yi aure, but... ni xan fi son mu ci gaba da xumunci da Hajiya Aisha as just the frnds we are, and marrying into same family, I mean relationship din mijinta da mijina, amma bana son xumuncin mu ya koma na in-laws, its somehow, that aside Yusuf, kusancin inna da Imaan.... don't misunderstanding me plss son, kai ma inna kakar ka ce, amma gaskiya akwai matsala daga bangaren inna ka bar ni ma in ji da headache daya...." Yusuf ya girgixa kai yace "Kiyi hakuri Mum, I don't think all this u are saying is enough da xai sa ki hanani auren Imaan" Aunty ta bude baki tace "Ni nace xan hana ka aure Imaan Yusuf, idan Allah yyi Ita din matar ka ce ni na isa in hana? Don't quote me wrong plss, amma kai kasan kana son ta me yasa ko sau daya baka taba nuna alamar haka ba?" Yace "That's bcos she is still young, har yanxu Imaan bata san meye rayuwa ba, bata san kanta ba har ynxu, I was thinking idan ta fara jami'a ta d'an yi hankali sai in fito da intentions dina toward her" Aunty tace "Toh Allah ya kyauta, I think it's best ka je ka samu abbanku, amma ni nasan da kyar ne...." Yusuf yyi kasa da kai a hankali yace "Ni dai ki daina cewa haka plss mum, support me sannan ki min addu'a" a sanyaye tace "Toh na daina cewa haka, Allah yayi maku xabi mafi alkhairi Yusuf" yace "Nagode mum" daga haka ya mike ya nufi kofa ta bi sa da kallo har ya fita, Tagumi tayi tana furta innalillahi.... A xuciyarta. Sake baki Abba yyi yana kallon Yusuf with surprise, shi dai Yusuf bai yarda ya kallesa ba, bayan few seconds Abba yace "Yusuf" Sai a sannan Yusuf ya daga kai da kyar yana kallon Abban nasa, Abba yace "Kana nufin Imaan kake so?" Yusuf ya sunkuyar da kai a sanyaye yace "Ehh Abba" Abba yace "Ikon Allah" Shiru ne ya biyo baya na kusan minti biyu, can Abba ya daga wayarsa yyi dialing number Mujaheed har ya gama ring ba a daga ba, Abba ya ajiye wayar sanin yana gun aiki, Abba yace "I am happy hearing this son, but at the same time I am disturbed coz I made a promise to someone earlier, all the same don't worry, Allah xai shige mana gaba, tashi ka tafi" Mikewa Yusuf yyi ya nufi kofa Abba ya bi sa da kallo yana murmushi. Ko minti goma ba ayi da fitar Yusuf ba sai ga Umma ta shigo parlon Abba cikin shirin fita, har sannan Abba was still pondering at what Yusuf told him, kuma har ransa yake jin xai fi kowa murna da wannan hadin, Auren d'an sa da tillon 'yar d'an uwansa, tunanin yanda xai fara billowa al'amarin yake, first ya fara kiran D'an uwan nasa ya sanar masa sannan su tafi gun Mahaifiyar su ita ma su sanar da ita, yasan Daddy xai yi farin ciki da hadin shi ma, don fargabarsa a ko da yaushe gidan da only child din tasa xata fada da sunan aure, yasan Daddy na son imaan fiye da tunanin me karatu, he can do anything bcos of his only child, Umma Ta karasa cikin parlon tace "Alhaji kasan Mujaheed ya tura min kudi xan fara hada masa lefe, to yau xan fara shiga kasuwa" Abba na kallonta da mamaki yace "What? Lefe kuma? But he told me nothing about that" Umma ta d'an bude ido tace "Toh ba sae an gama hadawa ba xa a kinkimo maka ka gani, kar ya fada maka kayi tunanin ko so yake ka basa wani abun, wllh ban son ya daura maka ko wani nauyi ne kaga ba a dade da hidimar seeyama ba, tunda Allah ya hore masa xai iya komai shi sa kawai nace kada ya gaya maka sai na gama hada kayan a kawo maka ka gani, ba laifinsa bane shi ma ya so sanar da kai na hanasa, amma idan hakan ya bata maka rai kayi hakuri don Allah" Abba yace "Toh Allah ya rufa asiri..." Umma tace "Ameen, tun jiya naga kamar abu na damun ka, shine nace to mai kuma ya faru, idan ma inna ce don Allah a dinga hakuri, uwa ce... Sai ayi ta fatan a gama lafiya da ita, ya ci ace duk abubuwan inna ya xame maka jiki yanxu..." Abba yace "Haka ne" Umma ta xauna ganin maganganunta sunyi tasiri xuciyar Abba, murya can kasa tace "Toh me kuma take so Alhaji?" Abba yace "A'a wannan mun shawo shi tare da Sadeeq, Yusuf ne dai ya xo min da wata magana yanxu da ya kulle min kai... Am still trying to find a way out ne har yanxu" Da mamaki Umma tace "In ji dai lafiya??" Abba yace "Lafiya lau, yar uwarsa Imaan yake so da aure wai" Mikewa Umma tayi da mugun mamaki baki bude tana kallon Abba, can tace "Aure kuma Alhaji??" Abba yace "Kwarai, yanxu ma ya bar parlon nan" Umma tace "Ikon Allah.... Aure fa???" Juyawa tayi ta nufi kofa tace "Toh Allah yayi mana mai kyau dai, ya xaba abinda ya fi alkhairi, ae imaan yar uwar sa ce, Imaan ta mu ce..." daga haka ta fice, direct sama ta wuce ta bude dakin Yusuf ganin baya ciki ta shiga dakin Aunty, xaune ta samesa tare da Aunty, Umma tace "Amma Yusuf kayi asara wllh, ka kuma samu tabin kwakwalwa mai wuyar ganowa balle ayi maka magani, yanxu ka rasa warce xaka je kace ma Ubanka kana so sai Imaan, Yusuf me ya same ka ni Rukayya?? ina ita Hafsar da kake nema take??" Yusuf dake kallonta yace "Umma ni Hafsat ba aurenta nace xan yi ba" Salati Umma ta saki tace "Amma Allah ya isa tsakaninmu da kai, mu xaka ka ma bakin ciki Yusuf?? ka bar 'yar attajiri ka dawo kace mai lalura iri iri kake so? Anya akwai lafiya kuwa, mu xaka kwaso wa mugun iri, irin ciwo a xuri'ar mu? Yarinya mutu kwakwai rai kwakwai?? Toh wllh tunda an asirce uwarka ta kasa cewa komai ni kam ba a asirce ni ba sai inda karfina ya kare in sha Allahu, yanda xan ma Mujaheed haka xan maka don duk daya ku ke a gu na, in sha Allahu sai naje na gano tushen abun nan... Ba wanda ya isa ya ci nasara a kanka kamar yanda aka ci a kan kanin Ubanka, uban kuturu yyi kadan wllh balle na makaho" daga haka ta fice a dakin kamar xa ta tashi sama, Aunty da ta bude baki tana ta kallonta tace "Ikon Allah ya fi gaban haka...." Daddy couldn't help it but laugh bayan Abba ya xo har part dinsa ya sanar masa intention din Yusuf a kan Imaan, Daddy yace "Ikon Allah, nayi farin ciki sosai sai dai kar ka mance da alkawarin da kayi a baya barrister, ko ya xa mu yi?" Abba yace "Sure ina sane, shi ma ba wai xa a dakatar da shi bane Sadeeq din, abinda xai faru yanxu kawai mu fara xuwa gun Inna mu je ta bakin ta kafin a yanke ko wani decision" Daddy yace "Gaskiya ne wannan" Part din inna suka tafi a tare, Inna ta fito daki tace "Tun safe in gaya maku nake aiki ban xauna ba, ku leka bandakina ku ga ko tuwo ya xube kasa xa a iya xaunawa a cinye tass, ba ku ji bayana ba kamar ya balle ni dai in huta" Murmushi duk suka yi suka xauna, Daddy yace "Gwara dai ki dinga hutawa haka inna, gashi kince baki son mai aiki balle a samo maki ko yar dattijuwa ce" Inna tace "Ni ko ina xan so masu aiki mutane duk wari, sannan su cinye ma mutum abinci, A'a ba ruwana ni ko da rarrafe ne xan yi aikina, 'ya yanku ne sun xama abun tsoro banda haka Imaan ko Maimoon ko Ummi baxa su dinga xuwa min d'an share share ba banda karshen duniya da lalacewa ta xo" Abba yace "Inna ke fa kika ce baki so, ai da suna xuwa..." Inna tace "Ehh ni nace bana so, don ba abinda suka iya gaskiya, basa min yanda nake so, ni dai nace na yafe su daina xuwa" Duk suka yi shiru basu ce mata komai ba, ganin ta dauko tsintsiya Abba yace "Inna daxu Yusuf ya sameni kan wata magana da naga ya dace mu sanar maki kafin mu yanke hukunci...." Ajiye tsintsiyar tayi ta xauna kan kujera da sauri tace "Me ya faru kuma??" Abba ya d'an yi murmushi yace "Wai yar uwarsa Imaan yake so da aure...." Inna ta gwalo ido ta saki baki tana kallonsu, saukowa kasa ta yi a hankali ta xauna kan rug ta fashe da matsanancin kuka tana tafe hannu tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, LA haula wala kuwata illa billahil Aliyul Azeem, la ilaha ilallahu Muhammadurrasulillahi sallallahu alaihi wassalam, hasbunallahu wa ni'imal wakeel.... Na ga abinda ya isheni ni patuuu" Daga Abba har Daddy kallonta suka dinga yi da mamaki, inna ta dakatar da kukan da take tace "Toh da kyar idan Imaan bata ta6a shan nonon Amina ba ma, yo ta ma sha ne kawai... Idan xa kuyi ta kanku kuyi ta kanku" *The book Imaan is not free, you read for free ur cup of coffee*🤷🏻‍♀️ It's 300 via Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah Then u show ur evidence of payment via my WhatsApp digit 07087865788 to be included in the payment group.Girgixa kai Daddy yayi yace "Hakan bai ta6a faruwa ba Inna, ko kin manta ba gida daya muke lokacin ba" Inna ta mike a fusace tace "Yau naga jaraba ni Asabe, ka fi ni sanin abinda nake ne Bukar, so nawa idan matarka xata fita gantalinta na makaranta take kai ma Amina Imaan, kuma babu wanda bai san irin kukan banxa da shagwaban da Imaan tayi tana jaririya, bata kuma yarda ta sha komai sai nono, shi sa ma bana son a kawo min ita ba ruwana, kuma kace min 6ata ta6a shan maman Amina ba?? karya xan xauna in giggilla maku da tsufa na?" Sai kuma ta fara kuka ta xauna tayi tagumi tace "Shkkn karshen duniya ta kama....." Abba ya sauke ajiyar xuciya yace "Toh bari a kira Aminar a tambayeta" Kuka kawai inna take bata tanka su ba, Abba ya dau waya ya kira Aunty, bayan ta daga yace "Ki taho part din inna yanxu, it's urgent" tana tambayarsa abinda ya faru bai bata amsa ba ya katse wayar, Aunty tayi jigum dama ita irin abinda take gudu kenan, haka dai ta sa Hijab ta fita xuwa part din inna, Daga Abba har Daddy sai kallon inna dake sharban kuka suke, da daddy yayi kokarin bata hakuri a fusace tace "Rufe min baki, naki hakura, ko dole ne?" Haka yasa duk suka ja bakinsu suka yi shiru, da sallama Aunty ta shiga parlon inna, Abba da Daddy kadai suka amsa mata, banda Inna dake hararanta ta gefen ido, Aunty ta durkusa tace "Ina kwana Inna?" Inna tace "Sai yanxu garinki ya waya da xaki ce min ina kwana? Ina ce ana idar da sllhn asuba nan ya kamata ku yo ku gaisheni amma ke da Aisha sai rana tayi gauuu sannan ku yo min nan wai kun xo gaisheni, ni dai ba ruwana a dinga jin tsoron Allah" Aunty dai ba ta ce mata komai ba sai gaida Daddy da tayi ya amsa, Abba yace "Amina wai kin ta6a ba Imaan mama?" Da mamaki Aunty ke kallonsa tace "Imaan kuma?" Abba yace "Ehh" Aunty tace "Ta ya hakan xai faruwa kuwa? A'a ni ban taba ba..." mikewa inna tayi, tayi mitsi mitsi da ido tace "Toh bari ku ji... da ki bata mama da kar ki bata duk uwarsu daya ubansu daya a wajena... in dai da rai na a duniya to wllh Isuhu baxai auri Imaan ba, harammm, ga dai d'an Bulasawa da ya riga sa sbda ku ba yan gaskiya bane shine ku ke son yi masa fin karfi, to ni 'yar gaskiya ce, kuma ba a cin amana da ni, na kuma yi ma yaron alkawari Imaan ta sa ce, don haka duk ku yi ta kanku munafukai kawai, shi isuhun tun da can bai san yana sonta ba sai da ya ga bulaswa sbda bakin ciki da hassada kar jikata ta huta, to aniyarsa ta bi sa, to wai ma ina figaggiyar budurwarsa da har xai ce sai jikata sbda rashin tsoron Allah, to ni ba ruwana ya cire idonsa kan jikata na riga na mata miji" sai kuma ta fashe da kuka ta rike kai tace "Innalillahi Wa inna ilaihi raji'un, wayyooo ubangijina, su dai yan gidan nan basa tsoron Allah na rasa me yasa haka, basa tsoron axaban Allah, xaman gidan nan ya haramta gun mai tsoron Allah iri na, ni dai idan xuciya ta kwasheni ma sai in tafi Habuja gun shegen Balan can inyi xamana, don wani lkcn ma gwara 6are da naka" Mikewa Daddy yyi ya nufi kofa ya fita parlon, Aunty ta tashi ta bi bayansa, A hankali Abba yace "Toh kiyi hakuri an bar maganar in sha Allah inna" Ta kunce habar xaninta tana share idonta tace "Ni dai ba ruwana, tunda haka isuhu ya xama dama kar ya sake tako min nan, gwara min Mujaheed sau sittin a kansa, shi Mujaheed baya haka, xuciyar sa mai kyau ce, kuma ni duk wanda ya sake tada maganar nan gaskiya xan ja masa Allah ya isa" Mikewa Abba yayi yace "Sai anjima" ko tanka sa bata yi ba har ya fita ya kulle mata kofar. Abba ne xaune parlonsa da Daddy sai Aunty, Yusuf ma na xaune kansa a kasa, a hankali Abba yace "Kayi hakuri Yusuf, Allah ya sa hakan shi ya fi maka alkhairi" Yusuf ya daga kai ya kallesa yace "Ameen" Daddy kam kasa cewa komai yayi, Aunty ta mike ta fita parlon. Misalin karfe goma da rabi na safiyar ranan Imaan ta fito parlor bayan tayi wanka ta shirya cikin atamfa an mata dinkin riga da skirt da ya amsheta sosai, gaida Daddy dake parlon a xaune tayi, he was still tensed at what happen safiyar ranan, bai taba tunanin Inna xata yi masu haka ba, gaba daya bai ji dadi ba, don ko da ace yau Yusuf bashi da hali bai ci tayi haka ba sbda shima jikanta ne, balle Yusuf is perfect in every aspect, ko Ammi daddy ya kasa gaya ma, ya kalli Imaan ya amsa gaisuwar da tayi masa, ta mike ta wuce kitchen gun Ammi, Ammi tace "Ki dau nose mask ki sa ki tafi ki share balcony din nan ki goge it's too dusty ni kuma xan tafi unguwar rimi yanxu ina sauke girkin nan" Ta marairaice tace "Ammi toh ai nima can xanje fa yau, gashi har na shirya" Ammi tace "Me xaki je kiyi biki saura kwana uku???" Kamar xata yi kuka tace "Don Allah Ammi ki bar ni in je, Anty Halima fa kawata ce kawai don dai ta girmeni ne, plss Ammi let me go" Ammi tace "A'a ba ruwana sai daddy ya bar ki, yanxu ki tafi ki share min inda na sa ki" A Hankali ta juya ta fita kitchen din ta tafi daki ta dauko thick nose mask dinta ta dau sweeper xata fita daddy yace "Ina za ki?" Tace "Xan share waje ne" Daddy yace "Xa ki share waje kuma? Ina mamar taki?" Ammi dake jin su a kitchen ta leko tace "Gani!!" Daddy yace "Ta share k'ura fa kika ce madam" Ammi tace "Ga dai nose mask nace ta sa ae, toh wai yallabai idan tayi aure ni zan bi ta ina share mata gidan ko kuwa haka za ta bar gidanta ba tsafta sbda tana da asthma??" Daddy dai bai ce komai ba, Imaan ta juya ta fita, daddy ya juya yana kallon Ammi yace "Ba lallai tayi aikin gida ba idan tayi aure, I will get her a housemaid that's capable" murmushi Ammi tayi tace "Lallai kam, to idan mijin yace bai son Housemaid fa?" Mikewa daddy yyi yace "Sae a fasa auren, I know what I am saying...." daga haka ya wuce dakinsa, Ammi ta tabe baki ta juya ta koma kitchen, Imaan na share tiles din dake shimfide a babban balcony din nasu lkci lkci xata mike ta d'an huta idan ta ji breathing din nata na sarkewa, kamar ance ta juya taga Mujaheed kai kana ganinsa kasan daga asibiti yake, mikewa tayi tsaye ta jingina da pillar tana sauke numfashi a hankali, Mujaheed ya tsaya yana kallonta coz she looks so tired, fuska daure yace "Wa ya sa ki shara?" Ba tare da ta kallesa ba tace "Ammi" d'an jim yyi sai kuma yyi wucewarsa part din inna, Xaune ya tadda inna a parlor fuska a tsuke, ya tsaya bakin kofa yace "Me ya faru kike kirana??" Tace "Baxan kiraka ba Mujaheed, naga xama bai gan ni ba na tashi naje na sami mai gadi ya nemo min lambarka ya kira min kai, ni dama kai ne nawa, da kai muke kashe komai mu rufe, tunda ga irin 'ya yan da Allah ya jarabce ni da samu, ni ba din ba din ba ma sai ince banyi dacen 'ya ya ba, samm Bukar da Ahmadu ba yaran nunawa bane" Kallonta kawai Mujaheed yake, can ya karasa cikin parlon ya xauna yace "me ya faru?" Ta fara matsar kwalla tace "Wai kaji fa Isuhu ya fito masu da cewar yana son Imaan da aure" a hankali Mujaheed ya mike yana kallonta da manyan idanuwansa, Inna tace "Maimakon su tsigale sa su masa tatass, tunda ga yaro d'an kirki na nemanta da aure, in gaya maka sai yaran nan suka biye sa, suka kwaso jiki suka yo min nan suna washe min hakora a can" ta fadi haka tana nuna masa kujeran da su Abba da daddy suka xauna, A hankali Mujaheed yace "Sai kika ce masu me?" A fusace tace "Me kuwa xan ce masu Mujaheed?? Balbalesu nayi nace ko bayan raina bulaswa xa a ba ma imaan, don ni yar gaskiya ce ba a cin amana da ni, kai kaji bakin ciki irin na d'an uwanka fa?? Shi mai daukan albashin da bai wani taka kara ya karya ba xai ce xai auri jikata taje ta mutu in shiga uku in lalace? Dududu albashin nasa ya wuce dubu dari biyu da wani abu?? A'a ba ruwana, ni dai nan na binne maganar nace bana son a sake tada ta ko inyi Allah ya isa, Imaan ta Bulasawa ce idan Allah ya yrda, shine abun ya min ciwo na fita na kiraka ina kuka a waya, ko kai ya ka gani?" Mujaheed ya sauke wani boyayyen ajiyar xuciya ya xauna yace "Haka ne, tunda ya riga sa" Inna tace "Atohhh... kai dama duk ka fita daban a jikokina, kai d'an gaskiya ne kamar ni, nasan kuma kai baxa ka ta6a irin wannan kazamin tunanin ba wai xaka auri Imaan, kai kaji wani sa6o don Allah a ja mana fushin ubangiji, toh Isuhu dai ya xama abun tsoro, har abada kar ya sake yo min nan don xan tsallake in gudu gidan bala" Mujaheed dai bai ce komai ba don har sannan gabansa bai daina faduwa ba ya rasa dalili, Inna tace "Ahmadu da Bukar dai sun xama shashashai yan cin amana, Allah ya shirye su, kuma su gaggauta tuba ga Allah ni ba ruwana" Mujaheed ya jinginar da kai da kujera ya lumshe ido a hankali, inna tace "Baka rufe ido ba wannan abun takaicin Mujaheed, Wllh yanda kake ji haka naji nima daxu, naji kamar ince wayyoooo Allah, kawai na fashe da kuka bayan fitar su, haka kawai suje su ja mana girgixan kasa a gidan" Mikewa inna tayi tace "Har naji sanyi da na gaya maka wllh, ni dai bari in kada shayina in sha, ba ruwana da wahala" Daga haka ta shige kitchen, Mujaheed ya dafe kansa, lkci daya ya dago yyi murmushi, da cup biyu ta fito tace "Ko kai ma in kada ma ka shayin ne?" Mujaheed ya kalleta yace "Toh" Imaan ta gama goge balcony din ta tafi cikin parlor tana cire mask din bakinta, Breakfast Ammi ta mika mata a tray ta ajiye ma Daddy a dinning table, karasawa tayi ta amshi tray din tana ajiyewa dinning sai ga Daddy ya fito, imaan na kallonsa ta marairaice a hankali tace "Daddy xan je gidan gwaggwo yanxu, sai in dawo bayan bikin Aunty Halima" Daddy ya ja kujera ya xauna yace "A'a sai dai ku dinga xuwa kuna dawowa da mamarki" Ammi tace "Sae kace handbag, kawai ka barta ta tsaya can har bayan bikin mana" yace "kin dai fi ni sanin condition dinta, so I don't need to talk much" Ammi tace "Imaan fa ba yarinya bace yallabai, she can take very good care of her self" daddy bai kuma ce mata komai ba. Duk yanda Ammi ta so Imaan ta jirata su fita tare kin yarda tayi don tuni ta kira Sadeeq bayan daddy ya amince ta tafi gidan gwaggo ta sanar masa, sai gashi ko 15 mins ba ayi ba ya kirata wai yana saman layin nasu yana jiranta, Ammi ta dinga kallonta da mamaki ganin ko gama rufe karamin trolley din bata yi ba amma xata ja haka ta fita, cikin tsawa Ammi tace "Wai saurin uban me kike haka Imaan??" Waigowa tayi da sauri tace "Ba komai fa Ammi" Ammi tace "Rashin natsuwa ce kenan, ke kam yaushe xaki yi hankali ne irin na sauran jama'ah, dubi fa yanda kike jan jaka a bude saboda hankali ya maki kadan" Daddy dake xaune dinning yace "Komai dai ace sai anyi fada, this isn't fair" Ko tanka sa Ammi bata yi ba, Imaan ta durkusa a hankali ta karasa rufe jakar, Ammi tace "toh xaki iya daukar jakar har bakin titi?" Imaan tace "Ai ba nauyi Ammi, kuma ja xan yi tunda titin layin na da kyau" Ammi tace "Toh Allah ya kiyaye" daga ma Daddy dake kallonta hannu tayi ta fita, ta rufe kofa kenan sai ga Mujaheed ya taho daga part din inna, kallonta ya dinga yi tayi saurin dauke kai gabanta na faduwa, kallon Sashin su yyi sannan ya kalleta yace "Ina xa ki?" Backing dinsa tayi, tayi kamar tana gyara jakar ne ta turo baki tace "Gidan gwaggwo" Jin bai ce komai ba ta leka sa daga durkushen da take, kallonta taga yake yi har sannan ta kara turo baki, jin tafiyarsa ta saci kallon gefenta taga gate ya nufa, sai da ta jira taga fitarsa gaba daya, bayan few minutes ta ja jakarta ta xuwa gate, tsaye ta gansa jikin motarsa ya rungume hannu, gabanta yayi mugun faduwa, ji tayi kamar ta rushe da kuka, tayi saurin dauke kai xata nufi saman layin yace "Xo ki sa jakar a mota" Da sauri ta kallesa sai kuma ta fashe da kuka ba hawaye tace "Yaya Ammi da Daddy fa cewa suka yi in tafi da kai na kar wanda ya kai ni wllh" Wani mugun kallo ya mata yace "Before the count of 3 do what I said now" jingina tayi da gate hankali tashe tace "Don Allah yaya ka wuce wllh bana son ka kai ni xan je da kai na" hade rai yyi sosai ya daga finger dinsa daya yyi indicating da one, sannan two, bata jira ya nuna third finger din ba ta ja jakar hawayen gaske na xubo mata ta bude back seat ta ajiye ta rufe, cikin rawar murya tace "Xan dauko hand bag dina" bai tanka ta ba ya xaga ya shiga driver seat ta koma cikin gidan ta fashe da matsanancin kuka, parking space ta tafi ta tsaya ta yi dialing number Sadeeq, yana fara ring ya katse ya kira ta, ta kai kunne cikin sanyin murya tace "Don Allah kayi hakuri Yaya xai fita aiki yanxu shine yace xai yi dropping dina, ni kuma baxan iya cewa A'a ba kar ya min fada" Sadeeq yace "Ohk no problem imaan, anjima da yamma xanje can gidan in sha Allah" a hankali tace "Kayi hakuri don Allah" yace "Noo ba komai dear, ai yaya ne, kar mu yi laifi ko" tace "Toh nagode" daga haka yyi mata sallama ya katse wayar ta nufi gate fuska daure ta fita, bude motar tayi ta shiga tana cika tana batsewa, ta gefen ido ya kalleta ya tada motar ya bar layin. Sun yi nisa sosai kamar mai counting words dinsa yace "I told u what to tell Abba... but you told him a different thing saboda kin raina ni koh?" A d'an tsawace ya kare maganan, Kin cewa komai tayi sai ma kauda kai da ta yi tana kallon waje, parking yyi ganin haka ta juya da sauri tana kallonsa kamar xata yi kuka tace "Don Allah kayi hakuri yaya, ai ya ma daina kirana, tun shekaranjiya ni bai kira ni ba ma" Fuska daure Mujaheed yace "In ga wayar ki?" Xaro ido tayi tace "Yaya ai yana gida" tana magana tana kokarin boye wayar a jikinta, fixgota yyi, ta yi wani kara ta riko hannunsa tace "Wayyoo yaya me nayi maka..." Ya dage Hijab din jikinta ta xaro ido tace "Yayaaa ka bari" bai saurareta ba har sai da ya kwace wayar, dubawa yyi yaga ta sa password, ya mika mata yace "Bude..." Make kafada tayi tana wani murmushi, ya dinga kallonta kafin ya daura wayar kafarsa ya ci gaba da driving din, har suka iso gidan gwaggwo bai sake ce mata komai ba, ita ma bata ce masa komai ba, yayi parking kofar gidan, bude motar tayi ta fita, shi ma ya fito, ta bude back seat ta dau jakarta ta rufe motar, danna lock yyi ya wuce cikin gidan ta bi sa da kallo kamar xata yi kuka, can ta bi bayansa, Gwaggwo ce xaune parlor tare da wasu yan uwanta duk maxa, Mujaheed ya xauna kasa ya gaisheta sannan su ma ya gaishe su, Gwaggwo da fara'a Gwaggwo ta amsa tana cewa "Ikon Allah, yau Mujaheed ne gidan namu, dama kana garin Mujaheed" ya d'an yi murmushi yace "ina nan Gwaggwo ya kwana da yawa" tace "Lafiya lau... Ka guje ni Mujaheed" Har sannan yana murmushi yace "Kiyi hakuri gwaggwo yanayin aiki ne, xan je anjima da yamma in dawo tun da kina da baki" Imaan ta xaro ido jin abinda yace, Gwaggwo tace "Ka tabbatar Mujaheed" yace "Xan dawo da gaske" tace "Toh madallah, sai ka dawo, Allah ya kiyaye hanya, ina nan ina jiran ka" Imaan dai na makale jikin kofa ta ki shiga gidan, Mujaheed ya fito, kallo daya yyi mata ya dauke kai ya nufi gate, ta bi sa da sauri tace "Don Allah yaya ka ban wayata" wani kallo da ya tsoratata ya mata, ta koma baya a hankali, ya nufi gate ya fita gidan. Tun da yamma yayi hankalin Imaan ya tashi, tasan yanxu kila Sadeeq ya kira ta wayar Mujaheed kila kuma ya daga, sannan ga Ammi tana gidan, duk abun ya taru ya mata yawa, ita kadai ce kwance dakin Gwaggwo don anty Halima na tare da kawayenta, ana idar da la'asar sai ga Halima ta shigo dakin ta mika ma Imaan wayarta tace "Imaan gashi abokin ya Muhsin xai maki magana" da sauri Imaan ta mike daga kan darduman da take xaune bayan ta idar da sllh ta amshi wayar Anty Halima ta juya ta fita, xaunawa tayi gefen gado tayi masa sallama a hankali, ya amsa yace "Is ur fone down?" Xaro ido tayi da farko ta rasa abun cewa can tace "Um, ka kira a kashe koh?" Yace "Sure" ta langwabar da kai tace "Ehh a kashe yake" yace "Ohk, ina waje fa" ta wani xaro ido again, a hankali tace "Toh ina xuwa" yace "Ohk I am waiting dear" mikewa tayi ta fita, rasa wanda xata gaya ma ana kiranta a waje tayi don tsoron sanar da Ammi take, gwaggwo ta shiga nema, ta sameta a Wani empty room tare da Ammi da maman Halima, ta gaida maman Halima da ta amsa mata da fara'a tace "Ya Abban ki Imaan?" Imaan tace "Yana lafiya mama" daga haka ta nufi gun Gwaggwo ta durkusa murya can kasa tace "Gwaggwo wai Sadeeq yana waje yana jirana" Ammi dai sai kallonta take don bata san abinda take gaya ma mahaifiyar tata ba, Gwaggwo tace "Sadeeq dai da na sani abokin Muhsin?" Imaan ta sunkuyar da kanta, Gwaggwo tace "Ikon Allah, saurayin ki ne kenan" imaan ta boye fuskarta, gwaggwo tayi dariya tace "A'a gaskiya naji dadi, Sadeeq ai yaro ne mai hankali da sanin darajan mutane, tashi ki tafi ina gaishesa, ko kwana uku da suka wuce ya xo gaisheni da Muhsin, gaskiya nayi farin ciki da wannan al'amarin" Ammi dai sai kallon Imaan take, mikewa imaan tayi a hankali ba tare da ta yarda sun hada ido da Ammi ba ta fita, tana fitowa parlor ta ji sallamar Mujaheed, still tayi inda take tsaye, Gwaggwo na jin muryar sa tace "Ashe dai da gaske yake xai dawo" Mamaki ya sa Ammi ta kasa cewa komai jin muryar sa ita ma, mikewa Gwaggwo tayi ta fito parlor murmushi dauke fuskarta tana amsa sallaman tare da few mutanen dake parlon, shigowa yyi suna hada ido Imaan ta juya masa baya da sauri kamar xata yi kuka, ya nufi kujera ya xauna Gwaggwo na masa sannu da xuwa, ta kitchen imaan ta bi ta fice daga gidan. Sauke glass Sadeeq yyi ganin ta, ta sunkuyar da kai har ta isa jikin motar, ya fito ya jingina gefenta smiling cikin cool voice dinsa yace "Good evening" kasa kallonsa tayi, a hankali tace "Ina yini?" Yace "Lafiya lau Imaan, ya Ammi fa?" Ta kalli cikin gidan tace "Tana ciki" yace "Amma ba tare ku ka xo ba ai?" Ta girgixa kai tace "Na riga ta" har sannan ta ki yarda su hada ido, a hankali yace "Kinyi kyau sosai, I love the Hijabs you are wearing, you look so cute in them" boye fuskarta tayi tana murmushi, ya dinga kallonta, kamar warce ta tuna abu ta xame hannunta da sauri tace "Na manta na daura abu a kitchen kar ya kone" yace "Xa ki wuce ciki knn?" Cikin sanyin murya tace "Kayi hakuri, ai mun gaisa" ya d'an yi murmushi yace "Sure, amma ina son mu yi hira sosai, I told you I've got plenty things to let you know imaan" tace "Toh may be later koh?" Yace "After Magrib or Isha?" Ta gyda masa kai, yace "Ohk then, Allah ya kai mu lkcn, before then wait...." Yana fadin haka ya bude motarsa ya fiddo wani abu kamar box mai kyau yace "You put this on for the wedding" kin amsa tayi, gently yace "Take plss Imaan" ta kallesa a sanyaye, ya gyada mata kai murya can kasa yace "Take it" risinawa tayi ta amsa tace "Nagode" ya mata murmushin da ya bayyana dimples dinsa ta mayar masa da light murmushi sannan tace "Sai anjima" daga haka ta nufi gate ya bi ta da ido har ta shiga gidan, sosai gabanta ya fadi ganin Mujaheed ya fito parlon gwaggwo, ya dinga kallonta ta fara tafiya a hankali, kamar warce aka ture ta durkushe nan kasa ta fara yarfe hannu tana xaro ido, ya karaso inda take yace "Daga ina kike?" Hawaye har ya kawo idonta tace "Ammi ta aikeni, yaya na gurde kafar fa" bai tanka ta ba ya nufi gate fuskarsa daure, ta bi sa da kallo gabanta na faduwa ta dinga addu'ar Allah yasa Sadeeq ya bar layin, kallon box din da ta boye a Hijab ta dinga yi kafin ta bude a hankali taga babban dankunnen gwal mai kyau sai talli yake a kwance cikin fancy box din.... *The book Imaan is not free, you read for free ur cup of coffee*🤷🏻‍♀️ It's 300 via Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah Then u show ur evidence of payment via my WhatsApp digit 07087865788 to be included in the payment group.Mikewa Imaan tayi da sauri ta nufi cikin gidan tana waigan ko Mujaheed ya dawo har ta shiga ta kulle kofa, dakin gwaggwo ta wuce ta boye box din a cikin trolley dinta, tsoronta daya yanxu Ammi, bata san me xata ce ba idan ta ga dankunnen, bayan Magrib suna cin abinci tare da Anty Halima da wata kawarta, wayar Halima ya fara ring, dauka tayi bayan taga mai kiran ta kalli Imaan tace "Wai ina wayar ki?" A hankali Imaan tace "Yaya ya kwace min" Halima ta xaro ido tace "Saboda me?" Buda hannu Imaan tayi alamar bata sani ba, Halima ta mika mata wayar tace "Toh gama magana tukun" karba Imaan tayi ta kai kunne bayan ta daga hade da yin sallama, Sadeeq ya amsa mata daga daya barin yace "Har yanxu baki yi charge din wayar ki bane Imaan?" A hankali tace "Ehh" yace "But naga akwai wuta ai yanxu, ina ma anguwar" ta langwabar da kai tace "Wayar na gida fa" yace "Ohk after Isha xan kira ki, it's almost time now" tace "Allah ya kai mu" daga haka ya katse wayar, Imaan ta ajiye gefen gado, Halima tace "Haka kawai Mujaheed din ya amshe maki waya?" Tace "Ehh wai saboda abokin Muhsin na kirana" Bude baki Halima tayi tace "Toh shi ina ruwansa" Imaan ta buda hannu tace "Nima ban sani ba" Rabi'ah kawar Halima tace "Yayanki ne kuma?" Halima tace "Cousin dinta dai" Rabi'ah ta d'an bude ido tace "Toh ko son ki yake?" Still Imaan tayi tana kallonta da wani expression, can tace "Yaya ne fa... Yayana ne shi" Rabi'ah tayi dariya sosai tace "Wai yaya ne, to haka kawai baxai dinga hana ki waya da samari yana kwace maki wayar idan babu wani abu a kasa" Imaan ta ajiye cokalin hannunta a hankali tace "Abu kamar me?" Halima tace "Tukunna dae me yace maki da yaga Sadeeq din na kiran ki?" Imaan ta jingina da gado tace "Kawai ya hanani waya da shi ne, har blocking dinsa yyi ni kuma nayi unblocking dinsa, a gida ma da Abba ya kira ni xai tambayeni meye tsakaninmu da Sadeeq kafin in je ya sameni wai ince ban san sa ba" Dariya sosai Rabi'ah take, Halima tayi murmushi tace "Tabb, lallai Mujaheed" Imaan dai sai kallonsu take don bata san me ya basu dariya ba, Rabi'ah ta ajiye spoon din hannunta tana kallon Imaan da kyau tace "Toh wllh son ki yake...." Imaan ta xaro ido ta koma baya da sauri tace "Don Allah ki daina cewa haka plss, wllh yaya na ne fa, Anty Halima yaya fa ne" Halima tayi wani murmushi tace "As far as ba ciki daya ku ka fito da shi ba ki daina deceiving kanki Imaan Mujaheed son ki yake, so mai tsanani ma kuwa, ni dama tun lkcn da yake kawo ki nan few years back ina ganin irin kallon da yake maki nasan ba a banxa ba da abu a kasa, sannan kulawar da yake maki ko kanninsa basa samun haka, abinda Mujaheed ke maki a da ya wuce shakuwa ko so na 'yan uwantaka, ke dai ce ban san lkcn da xaki yi wayo har ki fahimci inda ya dosa, wai yaya ne... A'a ba yaya ba..." lkci daya hankalin Imaan ya tashi ta fashe da kuka sosai tace "Wllh ku daina cewa haka ba kyau, ni ba wani so na da yake yi, ina ce maku yayana ne fa, to taya xai so ni, ni kanwarsa ce fa..." Dariya kawai Rabi'ah take don imaan tayi mugun bata dariya nan kuma ta yarda har sannan Imaan na tare da yarinta ba kadan ba sannan ga ta only child shi sa abun ya taru ya mata yawa, Imaan ta mike da sauri ta fice daga dakin ta koma wani daki ta xauna kan gado maganganunsu na mata yawo a kai, fashewa tayi da matsanancin kuka ta fada kan gadon tace "Ni baxan ma kwana a gidan nan ba, ta ya xa a ce wai yaya na so na, wai yaya fa?? Allah ya kiyaye wllh" Imaan bata ta6a jin abu ya tsaya mata a rai irin abinda Halima da kawarta suka gaya mata ba, wai Mujaheed sonta yake, tabbb, ji tayi ita gaba daya duniyar ma babu wanda take jin haushi kamar Mujaheed din, duk da tasan baxai ma taba yiwuwa ace yana sonta ba, amma abinda suka gaya mata yasa ita taji bata ma son sa shi a ido, bata son ganinsa kwata kwata, lamo tayi kan gado very restless, aka bude kofar dakin ta juya da sauri, Halima ta shigo tace "Gashi Sadeeq ya kira" Imaan ta mike xaune a hankali ta amshi wayar ta kai kunne tare da masa sallama, ya amsa yace "I am outside Imaan" tace "Toh bari in fada ma gwaggo" daga haka ta katse wayar ta tafi ta nemo gwaggo ta gaya mata, Gwaggwo tace "Toh ya shigo mana ai ba kowa parlon ma, ce masa yayi shigowarsa kawai" Imaan bata ce komai ba ta sa Hijab dinta ta fita, tsaye ta gansa ya jingina da motarsa, ta karasa kanta a kasa ta tsaya keeping a enough distance tsakanin su, kallonta kawai yake, ita ko bata yarda ta kallesa ba, a hankali yace "What's wrong imaan you look disturbed" da sauri ta daga kai ta kirkiri murmushi tace "A'a ba komai fa, ya gida" yace "Lafiya lau" tace "Gwaggwo tace ka shigo ciki ba kowa a parlor" Yace "No ni baxan shiga ba kunyarta nake ji yanxu" murmushi Imaan tayi tace "Toh akwai kujeru a compound ai, shi ma baxa ka shiga ba?" Ya shafa kansa smiling sweetly yace "Ohk then mu je" ita ta shiga gaba ya bi bayanta har suka shiga cikin compound din. Sai da ta fara xama kan farin plastic chair sannan ya xauna shi ma yana kallonta, dauke kai tayi ganin kallon da yake mata yace "Amma ba dai kunyata kike ji ba" murmushi tayi tace "Shi nake ji mana" Yayi dariya yace "Aa kiyi hakuri kar ki ji plss" Ita dai bata ce komai ba, bayan few seconds yace "Did you know what imaan" ta daga kai ta d'an kallesa, cikin sanyin murya yace "I am hoping to spend the rest of my life with you" Imaan ta sauke idonta kasa, yace "I was born and bred in Uk, yawancin rayuwata duk can nayi sa, daga baya na dawo Nigeria gaba daya, I've neva for once thought xan hadu da mace yar Nigeria inji ina son rayuwa na har abada da ita sai kan ki Imaan, my ex was white ita ma it's not as if I have much feelings for her, it's just to while away time... Here in Nigeria frndship kadai ne tsakanina da yan mata, Ni ban san meye so ba, I don't even believe in it until I met you few months back, pls don't break my heart imaan, it's too fragile for something this big...." Imaan tayi murmushi a sanyaye bata dai ce komai ba, yace "Yea... I have been counting down tun yanxu xuwa ranan da xaku fara waec, but plss me yasa baxa kiyi waec din a ss2 ba" xaro ido tayi ta kallesa, yace "Sure, a lot a ss2 suke waec" tace "Aa nafi son inyi ss3" ya lumshe ido ya bude yace "almost a year to come in sha Allah kenan fa Imaan?" Imaan ta kallesa tace "Sure" yace "Toh Allah ya kai mu lafiya" Tace "Ameen" Yace "Promise me something plss...." Imaan tayi shiru tana kallonsa, yace "Ki min alkawarin baxa ki yi betraying din soyayyata gare ki ba, and I am also promising u same, I will and will neva leave u for any reason" lkci daya jikin Imaan yyi sanyi tace "Ae an riga an san ka gidanmu, so there is nothing to worry about" yace "Sure an san ni, but I am afraid of ur cousins" da mamaki tace "Cousins dina kuma?" Ya d'an yi murmushi yace "Yea kada su min fin karfi...." Imaan ta kasa daina masa kallon mamaki tace "Su ai yayyina ne ba so na suke ba" Sadeeq ya girgixa kai yace "I saw their reactions ranan da Abbansu ya kira ni, more especially the very fair one" Imaan gabanta ya shiga faduwa, Sadeeq yace "They might not tell you now amma kada watarana su xo su ce suna sonki ki mance alkawarin mu, kada ki min haka plss Imaan..." cike da damuwa ya fadi haka, imaan ta ji kamar ta fashe da kuka tace "Ni ka daina cewa haka, ba wanda ke so na cikinsu duk yayyina ne su wllh, they are only disturb sbda ban gama secondary schl ba" yace "Toh Allah ya sa haka, amma ba sai kin min kuka ba gimbiyata, reminder ne" Imaan ta boye fuskarta da Hijab, yyi murmushi yana kallonta, murya can kasa yace "Kin san inda xan kai ki for our honeymoon?" Kamr yace ta kara boye fuskarta da Hijab cike da shagwaba tace "Ni dai bana sooo" yyi dariyarsa mai dadin sauraro yace "Toh na bari baby, when the time comes xa ki ga, amma fa tare da kaka xa mu" da sauri Imaan ta bude fuskarta ta xaro ido tace "Aa ba inda xata bi mu" Sadeeq couldn't help it but laugh yace "Are you serious??" Ita kanta sai daga baya taji kunyar abinda ta fada ta mike da sauri xata wuce ciki yace "Noo plss wait dear, ki rakani first plss" da kyar ta yarda ta rakasa gate tana sinne kai, ya juya yana kallonta kafin yace komai, a hankali tace "Thanks much for the earrings na gode sosai" Ya mata wani kallo yace "Bana son ki min godiya idan na baki abu, ba don ki gode min bane na baki" murmushi kawai tayi bata ce komai ba, nan suka yi, sallama ta daga masa hannu ta koma cikin gida. Washegari gidan gwaggwo ya xamo ba masaka tsinke saboda yan uwa da abokan arxiki duk da gobe ne daurin auren, imaan dai na daki duk ta takura, ita dama haka Allah yayi ta bata da sakewa cikin mutane, babu yanda Halima bata yi da ita kan ta bi su gidan wata makociyarsu ba don can xata xauna har gobe sbda mutane amma taki, Har daki Ammi ta kawo mata abincin rana ganin ta ki fitowa, ganin yanda take yatsine yatsine Ammi tace "Ko dai xa ki wuce gida ne bana son matsala" girgixa kai tayi tace "A'a kawai kaina ke min ciwo amma idan na ci abincin xan sha magani" Ammi ta tabe baki ta fita dakin, imaan ta gama cin abinda xata ci a abincin ta dau maganin ta sha, mikewa tayi rike da plate din ta fita don kai wa wajen wanke wanke, tun da ta fito parlor taji numfashinta na tsarkewa ta dai dinga gyaran murya har ta fita compound, hayaki ne cike gidan saboda wutan icce da aka hura, ta rike numfashinta da sauri ta karasa ta ajiye plate din ta juya xata shiga parlor ta saki numfashin, tari ta fara sosai ta durkushe nan bakin kofa mutane suka taho kanta, Nan Asthma dinta ya tashi duk Gwaggwo ta rikice tana salati, Ammi ta wuce daki da sauri don duba inhaler dinta a jaka, Aunty da sauran mutanen wajen suka shigar da ita parlor. Har Imaan ta samu bacci dakin Gwaggwo bayan an rufe duk windows din an kunna mata fan Halima ta shigo sanye da Nikab a kan Hijab dinta ta durkusa kusa da ita tace "Sannu Imaan" bude ido tayi amma ta kasa cewa komai, ba kadan asthman yayi attacking dinta ba wnn lkcn don har sun yi niyyar tafiya asibiti sannan ya lafa, Kai kawai ta iya gyada mata, Halima ta dinga kallonta cike da tausayi, Can tace "Sadeeq ma ya kira har sau biyu, bari in kirasa ince baki da lafiya" Ita dai Imaan bata ce komai ba, Halima ta kirasa ya katse ya kira ta, tace "Ka kira daxu ina sllh, na taho gida yanxu na tarar ma Imaan din bata da lafiya" Yace "Subhanallah what's wrong with her?" Halima ta rasa me xata ce masa da farko don bata san ko yasan imaan na da Asthma ba, can tace "Gata nan dai a kwance bari in bata" mikewa Imaan tayi da kyar ta karbi wayar ta kai kunne cikin sanyin murya tayi masa sallama, cike da damuwa yace "What's wrong with you dear?" a hankali tace "Naji sauki" yace "But what happened, dama baki da lafiya ne?" D'an shiru tayi kafin tace "I had an attack..." Da mamaki yace "Are... you asthmatic?" Ta gyada kai kamar yana ganinta tace "Um" yace "Subhanallah, to Allah ya sauwake... is ur breathing now ohk?" Tace "Sure" yace "Xa ki iya fitowa yanxu?" Ta yi shiru, sai kuma a hankali tace "I will try" yace "Alryt gani nan xuwa" katse wayar yyi, ta koma ta kwanta, Halima na kallonta tace "Allah ya sauwake imaan" imaan ta d'an mata murmushi, Halima tace "ki rike wayar idan ya kira bari xan je ana jirana na sani" Imaan tace "Toh nagode" daga haka Halima ta mike ta fita, ba a dau lkci da fitar ta ba Gwaggwo ta shigo da cup din tea ta xauna gefen gadon tace "Sannu Fatima tashi ki sha shayi na hada maki" imaan ta mike xaune tace "Gwaggwo ai na ci abinci, a koshe nake" Gwaggwo xata yi magana sai ga Ammi ta shigo dakin tare da Aunty, aunty na kallonta tace "Sannu Imaan, ya jikin" imaan ta d'an yi murmushi tace "Na ji sauki Aunty" Aunty tace "Toh Allah ya kara lafiya" fita Aunty tayi don xuwa su ci gaba da aikin da su ke yi, Ammi na kallonta tace "Kirjin yyi sauki?" Imaan tace "Kadan kadan yake min" Ammi tace "Toh sannu, dama sai da daddy ya guji hakan, nima nasan kawai wahala xa ki xo ki kara min nan" Gwaggwo tace "Wani irin magana ce wannan Aisha, ita ta daura ma kanta ciwon ashe?" Ammi dai bata ce komai ba, imaan ta kalli wayar Halima da ya fara ring, Sannan ta daga a hankali ta kai kunne, satan kallon Ammi tayi, murya can kasa tace ma Sadeeq "Toh..." Daga haka ta katse wayar, Gwaggwo tace "Wa ye?" Imaan ta sunkuyar da kai tace "Ce min yyi yana waje" Gwaggwo tace "Sadeeq?" Imaan ta gyada mata kai, Gwaggwo ta kalli Ammi tace "Toh ko ya ajiye ta gida kawai... Ni xamanta nan bai kwanta min ba, ba a fara komai na girki ba fa ciwonta ya tashi, ina ga gobe da xa ayi girke girke" Ammi tace "Waye ya kira ki?" Imaan ta kasa cewa komai, Gwaggwo tace "D'an gidan Bulasawa ne..." Ammi tace "Bulasawa kuma?" Gwaggwo ta kalli Imaan tace "Ko bata san ki da shi bane??"Imaan tayi kasa da murya tace "ta san shi" Ammi tace "Na san sa a ina??" Imaan tace "Abokin ya Muhsin fa" da mamaki ammi tace "D'an Bulasawa ne dama?" Gwaggwo tace "D'an sa ne na cikinsa, yaro mai hankali da natsuwa yana yawan xuwa tare da Muhsin gaisheni, ban ma san suna tare da fatimar ba, akwai wani lkcn dai da ya xo ya sameta a nan, ko tun lkcn suke tare ban sani ba" Ammi ta kasa cewa komai sai kallon Imaan take, Gwaggwo tace "To tashi ki je, ki ce masa ya shigo ina nemansa" imaan bata ce komai ba ta mike da kyar ta sa Hijab ta fita, bayan fitarta Ammi ta xauna gefen gadon tana kallon mahaifiyar ta tace "Anya kuwa Gwaggwo, d'an wajen Bulasawa fa, ina shi ina Imaan kuma? Kinsan yaudara tayi yawa yanxu a rayuwar fa" Gwaggwo tace "Fal yaqul khairan auliyasmut... Bana son irin wannan maganan, Sadeeq bai yi kama da mayaudari ba kuma tun kan ya san imaan yake xuwa min tare da Muhsin, ba a taba cewa d'an mai kudi ne yaron, faram faram yake da kowa, ni dai har ga Allah ya min kuma xan yi farin ciki idan Allah yasa shi ne mijin imaan" Ammi dai ta kasa cewa komai har sannan bata daina mamakin wai Sadeeq yaron Bulasawa bane. Tunda Imaan ta fito Sadeeq ke kallonta, ta sunkuyar da kai tace "Ina yini" yace "Lafiya lau, ya jikin?" Tace "Na ji sauki" yace "Tablet kike sha ko inhaler kike amfani da?" Tace "Inhaler" ya d'an yi shiru kafin yace "Toh Allah ya sauwake" Tace "Ameen, Gwaggwo tace ka shigo" ya d'an buda ido yace "Da gaske" ta gyada masa kai, yace "But ba mutane a ciki" d'an murmushi tayi tace "Idan ka shiga xaka gani" Haka nan dai Sadeeq ya shiga gidan yana sinne kai, bayan sun gaisa da Gwaggwo, Gwaggwo tace "Ka taimaka ka ajiye fatima a gida Sadeeq bata ji dadi ba" yace "Toh In sha Allah Gwaggwo" bai jima a parlon ba ya fita bayan yayi sallama da Gwaggwo, imaan ta fito daga daki rike da trolley dinta tayi ma Ammi da Gwaggwo sallama sannan ta bi bayansa... the journey was silent, lta dai ta jinginar da kanta tana sauke numfashi a hankali, lkci lkci Sadeeq ke kallonta sai ya sakar mata lallausan murmushi, ita dai sai dai ta sauke idonta, dai dai gate din gidansu yyi parking, a hankali ta kallesa tace "Nagode" yace "How will I reach you ltr, ko xaki yi plugging fone naki idan kin shiga ciki?" Ta d'an yi shiru kafin tace "Ina wayarka" bata jira cewarsa ba ta dau tsadadden wayar sa dake ajiye ta yi dialing number din inna yana fara ring inna ta dauka kamar jira take tana cewa "Ni dai an dameni, tun safe nake aiki ban xauna ba wllh, waye kuma wannan" murmushi Imaan tayi ta katse wayar, Sadeeq ma yyi murmushi yace "Number kaka koh?" Ta gyada masa kai ta bude motar ta fita tana kallonsa, Fitowa yayi ya fiddo mata jakarta yace "Ki huta sosai idan kin shiga ciki plss" tayi murmushi tace "In sha Allah" yace "Alright dear, Allah ya kara lafiya" wucewa ciki tayi ta nufi part din Inna, inna ta dinga kallonta daga sama har kasa tace "Lafiya kika taho min nan da jaka??" Imaan tace "A'a ni daga gidan gwaggwo nake" Inna tace "To har na ji sanyi" Imaan dai bata tanka ta ba ta ajiye jakar ta cire Hijab din jikinta ta kwanta kan kujera, inna tace "Toh har an gama bikin ne kika dawo ko kuma bikin ne dai garau garau kika gudo?" Imaan dai bata ce mata komai ba, inna tace "Atoh, ni dama shi sa naki xuwa kwata kwata, ba ruwana inje in dawo da yunwan cikina, biki ba na yan gayu ba, kuma dama Habiba bata ce min tana aurar da jikarta ba, ni dai na bada dubu biyar a kai mata ban bi ta halinta ba, Allah ne xai bani lada" Wani bowl dake rufe inna ta bude Imaan dake ta kallonta ta leki bowl din daga kwancen da take taga nama ne soyayye a cike, inna ta saci kallonta suna hada ido ta mike ta wuce daki da bowl dinta, ba a wani dau lkci ba ta fito da bokitai, ta sa makulli a kofar dakin, Imaan tace "Fita xa kiyi kike sa makulli a dakin?" Inna tace "Baxan sa makulli ba sauro su cika dakin su sa min cuta in bar 'ya yana da wahala?" Tana fadin haka ta fita waje xata wanke bokitan da ta kwaso, Imaan na kallon film da ake a TV taji muryar inna tana cewa "Mujaheed kai me cewa inje bikin su gidan uwar Aisha to ga jikar gidan ma ta gudo daga bikin balle ni karere, ji dai yanda aka dinga facaka da kaji a bikin kanwarka, toh can ni nasan baxa su yi haka ba, abinda duk na san su, meye ban sani ba..." Da sauri Imaan ta mike xaune jin wanda inna ta ambata, Mujaheed dake ta kallon inna yace "Ke dai ki daina haka..." Inna tace "Ni akwai wanda ya isa hanani fadin gaskiya kuwa duk girman duniyar nan?? to duk ba wannan ba don bai shafeni ba, inji ka siyo min kazar da nace maka nake marmari" Mujaheed bai tanka ta ba ya nufi kofar shiga parlon, da sauri Imaan ta saka Hijab dinta ta rufe har kafarta ta kafe TV da ido, Mujaheed ya shigo parlon, kallo daya yyi mata ya ajiye ledan hannunsa ya xauna yana danna wayar hannunsa, Imaan ta ki yarda ta kallesa gabanta sai faduwa yake, gaba daya she was uncomfortable, Inna ta shigo tace "Allah maka albarka, kai kadai dama xance ka siyo ka siyo" kitchen ta tafi ta dauko plate biyu ta xauna kan tabarma tana gogewa ta bude ledan kazar ta raba biyu, daya nata daya nashi, can dai ta kallesa tace "Toh ita kuma warcan matar ya xa mu yi da ita, tunda ba da ita aka siyo ba" shi dai Mujaheed bai ce komai ba, Inna ta tabe baki ta dauko wani plate din ta dau cinya daya da tsoka daya ta dangwala a plate ta mika ma imaan tace "Toh gashi dai, ido guba...." Ba tare da imaan ta kalleta ba ta girgixa kai gently tace "A'a baxan ci ba" Kallonta Mujaheed ya dinga yi da mamaki, inna ma ta saki baki tana kallonta tace "Dama baki da lafiya shine kika yo min nan salon ace a nan ciwo ya tashi ni patuu?? don cuta kadai ke hanaki cin kaza ni dai na sani" Imaan bata ce komai ba bata kuma kalleta ba, can ta mike ta nufi kofa tace "Ni fa a koshe nake" daga haka ta fice a parlon. *The book Imaan is not free, you read for free ur cup of coffee*🤷🏻‍♀️ It's 300 via Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah Then u show ur evidence of payment via my WhatsApp digit 07087865788 to be included in the payment group.Imaan na kwance bedroom dinta dab da Magrib taji an danna bell, tashi xaune tayi don ita kadai ce gidan Ammi na can Unguwar rimi, daddy kuma bai dawo ba, can ta mike ta sa Hijab dinta ta nufi kofar a hankali tace "Waye?" Muryar Ummi ta ji tace "Aunty na kiran ki" Imaan ta bude kofar tana kallonta, a tare suka tafi part din da Ummi, Imaan ta wuce sama ta bude kofar dakin Aunty, Aunty ta fito bayi bayan tayi alwala tana kallonta tace "Ya jikin?" Imaan tace "Na ji sauki Aunty" Aunty tace "Ammi can xata kwana fa, sai ki dawo nan ki kwana ko ki tafi gun inna" Imaan tace "Xan je gun Inna" Aunty tace "Toh ga abinci ki dauka" ba musu ta durkusa ta dau warmer din da Aunty ta nuna mata, Aunty tace "Ki tabbatar kin sha magungunanki bayan kin ci abincin" Imaan tace "Toh sai da safe" daga haka ta bude kofa ta fita, a stairs suka hadu da Yusuf, suna hada ido ya dauke kai, tace "Lah ya Yusuf kayi tafiya ne, ban ganka 2 days ba" Yusuf na ci gaba da haurowa stairs din yace "Not at all" daga haka ya wuceta ta bi sa da kallo, can dai ta sauka ta bar parlon. Part din inna ta wuce ta sameta tana sllh, ta ajiye abincin hannunta a parlor ta fito bakin tap ta daura alwala ta koma ciki, tana idarwa ta koma kan kujera ta kwanta, inna ta gama addu'o'in da take tace "Toh wai me yasa kika baro gidan bikin kika dawo?" Imaan tace "Dama ba kwana naje yi ba" Inna ta tabe baki tace "Toh ita Rukayya taje gidan kuwa?" Imaan ta girgixa kai tace "A'a bata je ba" inna tace "Ikon Allah, Kice Amina ce kawai ta je?" Imaan ta gyada mata kai, inna tayi tagumi tace "Naga abinda ya isheni, tun da uwata ta haifeni ban taba ganin haka ba wlh, Rukayya bata da xuciya mai kyau sam, ko da yake abun na da tushe, kinsan lkcn da Bukar ya auro Uwarki bata da aminiya da ta wuce Amina, lkcn Amina tana nan wata yar duma duma da ita kamar ki latsa ta jini ya feso, toh a lkcn gida daya Rukayya da uwarki suka xauna sai dai kowa da sashensa kamar dai Wannan gidan amma ko rabin gidan nan bai kai ba, lkcn Ahmadu da Bukar na yaku bayi basu da komai sai wahala, tun ba yau fa suke son junansu in gaya maki, dama a haka kuma suka taso, toh kullum Rukayya bata da aiki sai neman fitinar uwarki a tsakar gida, kaii Gaskiya Rukayya ta dade tana hauka, ga uwarki mai hakuri bata biye ta, ga uwa uba kawaici, amma akwai ranan da xuciya ya debi Aisha ta nakada ma Rukayya shegen duka har sai da ta targada mata hannu, da kyar aka kwace ta hannun Aisha, ni dai ce ma Bukar da Ahmadu nayi duk su kora su gidan iyayensu ba ruwana, to sun fa mayar min da gidan 'yaya wajen dambe, a lkcn kuma kullum Amina sai ta xo gun uwarki, tun fa Rukayya bata san Amina xata aure mata miji ba ta tsaneta har xage xage sun ta6a yi da jefe jefen dutse, to ana_nan ana_nan Ahmadu ya kyallara ido ya ga yar duma duma Amina, to karewa ma gun Aisha ya amshi lambarta idan ba mantawa dai nayi ba, Rukayya na ji tana gani Ahmadu ya aure kawar makiyiyarta wato Aisha, in gaya maki Aisha ce a kan gaba na komai da bikin, kuma ni nasan da gayya tayi haka, to da Aisha ma aka raka Amina dakinta gashi gida daya ya hade su da Rukayya, to kinji musabbabin komai... Ba irin xugar da Rukayya bata min ba kan in sa ubanki ya kara aure tunda uwarki bata haihuwa ni dai naki, kinsan da Rukayya yar dakina ce kafin ta xama bala'i, duk da dai nayi masa magana na yi masa magana har na gaji na kyalesa wato Bukar, to Aisha ta shanye min shi, daga karshe dai Bukar ya raba fada ya dauke uwarki suka koma Abuja da xama gaba daya, ai sun fi shekara biyar a Abuja, kuma fa lkcn... Katse ta Imaan tayi tace "Toh ni dai ban tambayeki ba, wllh har na gaji da jin labarin nan, a wata sai kin bada labarin nan ya fi sau biyar" Inna tace "Ai ba sai kin tambayeni ba duk sanda na ga dama dole in bada labari ko da kuwa ni daya ce a daki, to ina ruwan wani da ni??" Imaan ta tabe baki ta mike ta jona ruwa a heater don yin wanka, dawowa tayi ta xauna tana jiran ruwan yayi, inna tace "Ke wai bulasawan na maki waya ma kuwa?" Imaan tace "Ehh" inna ta d'an yi murmushi tace "Toh madallah, gama wanka ki xo in baki wani labari mai ban al-ajabi" imaan tace "Ai ruwan bai yi ba ki bani" Inna tace "Ki dai yi wankan tukun" Juye ruwan Imaan tayi haka ta wuce bayi inna na cewa "Don Allah idan kin gama ki dauraye bayin da omo, kazanta dai ba kyau" Imaan dai ba ta tanka ta ba ta cire kayanta ta shige bathroom. Imaan na gama wanka ta fiddo daya daga sleeping wears dinta dake press din inna ta saka ta feshe jikinta da turarrukan Inna ta fito ta xauna tana kallon inna da ke xuba gyangyadi a xaune, murmushi imaan tayi ta dau remote xata canxa tasha aka bude kofar parlor da sauri ta mike xata gudu xuwa daki Mujaheed ya shigo, tuni ta shige daki ta sa makulli ta wani hade rai, Inna da ta bude ido a gigice tace "Subhanallahi, lafiya??" Mujaheed dai na tsaye sai kallon kofar dakin yake, inna tace "Ni dai ba ruwana, ku dinga jin tsoron Allah, ya xa a maida min gida kamar filin daga, baka ji yanda xuciya ta ta tsinke ba wllh, ni dai ana shiga hakkina... Wnn 'ya ta Bukar dai ba ta da imani an wani laka6a mata Imaan din karya" Shi dai Mujaheed bai ce komai ba bai kuma fasa kallon kofar dakin ba, wayar inna ya fara ring, kamar xata yi kuka tace "Kaga wani bala'in koh, toh meye wnn fisabilillahi tsakar dare kuma" daukar wayar tayi ta danna inda ake picking ta kai kunne hade da sallama tace "Waye??" Sadeeq yace "Ina yini kaka?" Tace "Ce maka nayi waye??" Yace "Sadeeq ne" Inna ta bude ido sosai tace "Bulasawa?" Yayi murmushi yace "Ehh kaka" Inna tace "Lahh ina yini??" Mujaheed couldn't stop looking at her da mamaki, Sadeeq yace "Ya gidan kaka?" Tace "A'a lafiya lau wllh Bukar, ya iyayen ka?" Yace "Suna lafiya lau" inna tace "Toh madallah, shiru shiru ban ganka ba kwana biyu, Hala imaan ce ta baka lambar wayata?" Yace "Ehh ita ta ban" Inna tace "Toh ai ta kyauta wllh, shkkn sai in ba Mujaheed da ya tsaya kaina sandandan ya min saving, yaushe xaka billo?" Sadeeq yace "Gobe in sha Allah" Inna tace "Toh Alhmdllh, da kaina kuwa xan maka tuwo da miyar taushe in sha Allah" Sadeeq yayi yar dariya yace "Toh nagode kaka, imaan din na kusa?" da sauri inna ta mike tace "A'ahh toh bari in bata har ta kwanta ina jin, Kasan bata dade da dawowa daga gidan bikin su kakarta ta wajen uwa ba" Sadeeq yace "Toh ki barta gobe xan kira in sha Allah, dama ke na kira mu gaisa" inna tace "Ae ko naji ddi Allah maka albarka, maxa kashe kudin ka na ta konewa" yyi murmushi ya katse wayar. Inna na kallon Mujaheed ta mika masa wayar tana washe baki tace "Kai yi min saving, lambar bulasawa ne" Mujaheed ya amshi wayar yana kallon number, Inna ta xauna tace "Kai amma yaron ya kyauta, wllh na ji dadi, kaga alamar xai rike min jika da kyau kenan wllh, gashi gobe yace zai shigo, sai in baka dari biyar dita ka shiga kasuwa ka siyo min kayan miya da nama lafiyayye in masa miya mai kyau" Mujaheed ya xauna kan kujera har sannan bai daina kallonta ba, tace "Ka min saving mana Mujaheed kar lambar ya bace" Mujaheed ya gama danne dannensa ya mika mata wayar ta, ta amsa ta ajiye tace "Dole in tashi da sassafe kenan gobe, bari ma in dauko maka kudin kar ka manta ka tafi baka amsa ba in rasa d'an aike" Mujaheed dake kokarin controlling temper dinsa yace "Ki dai ba Yusuf" inna ta gwalo ido tace "Waye kuma Yusuf?" Mujaheed bai tanka ta ba tace "Toh bari kaji, Rabonsa da ya tako nan ya gaida ni tun ran da yyi abun kunyar nan, to dama idan ya xo da wani idon xai kalleni, A'a ba ruwana ni bana bukatansa dama, ga dai ka" Mujaheed na gyada kai yace "Ita kuma yarinyar nan kice mata wllh idan ta sake ganina ta kwasa a guje sai na sa ta kuka a gidan nan" inna tace "Oh oh Allah, yau naga jaraba, baxata gudu ba kana cutar ta Mujaheed? nine fa na koya mata ta dinga gudu idan ta ganka, toh me xata tsaya ta maka idan ta ganka, ni dai ba ruwana, ka dinga tsoron Ubangijin ka, ai ta ma kusan aure ta huta da fitinar ka sai in ga ko gidan mijin xaka bi ta kana cuta kuma, karshenta sai ka kare a kurkuku don Bulasawa daure ka xai yi a fita da kai kasashen turai ai maka hukunci, ka ga sai ka bar Ahmadu da Bukar da kashe makudan kudaden da suka fi karfinsu, idan ba haka ba kuma ka ru6e a kurkuku in shiga uku" mikewa Mujaheed yyi ya nufi kofa fuska daure, inna tace "Toh kudin cefanen pa, baka amsa ba fa? Ko xaka siyo min da kudin ka" Washegari da safe Imaan na shan shayin da inna ta hada mata, inna tace "Wai me yasa kike gudun katon can ne, halan laifi kika masa" Imaan taki cewa komai da farko, can kuma tace "Ba komai, ni bana son yana kulani a gidan nan nima kuma na daina kulasa, don Allah ki taya ni gaya masa inna" on a serious note ta fadi hakan, Inna tace "Toh ai hakan yafi ma, kinga babu ta yanda xai dinga cutarki kuma, wahalan da yayi a kanki a baya Allah ya saka masa, idan kuma biyansa yake son ayi sai ya fada min nawa ne bai gagareni in daga daya daga gidajena na gado in siyar in biyasa ba, kuma ba karamin aikin Bulasawa bane ya siya min wani ma a kasashen turai in xuba yan haya" Murmushi imaan tayi ta mike ta dauko mata dankunnen da Sadeeq ya bata, inna na budewa tace "Wannan ai gwal ce, a ina kika samo Imaan?" Imaan tace "Shi ya bani" Inna ta xaro ido tace "Mujaheed din???" Imaan ta hade rai tace "Sadeeq dai" Inna ta saki wani kabbara tace "Kinga abinda nake nufi ko, to a xamanin nan wa xai ma naka haka?? Wllh ki rike yaron nan da kyau kai ko su Maimoon kada ki yarda su san abinda kike ciki balle wancan mutumin Mujaheed, 'ya yan Ahmadu ba wani tsoron Allah garesu isasshe ba, duk yan bakin ciki ne, ki bar wannan gu na in ajiye maki, ana nuna ma su Ahmadu dama cewa xa su yi a mayar tunda ba hankali ya ishe su ba, shi ma mutumin nan Mujaheed yanxun nan xaki ga ya shigo wai gaisheni bai san ni damuna yake ba, maxa dauka ki wuce da shi ciki kada...." Bata rufe baki ba aka bude kofa, Abba ya shigo da sallama Mujaheed na biye da shi, Inna ta boye dankunnen a karkashin carpet, a hankali Imaan tace "Ina kwana Abba" Abba yace "Lafiya Imaan, naji baki da lafiya, ya jikin naki?" Kallonta Mujaheed yyi da sauri, tace "Naji sauki Abba" Abba yace "Toh Allah ya sauwake" tace "Ameen" kallon inna tayi tace "Inna zan je dauko kayana" inna tace "Toh yi maxa" tashi tayi ta nufi kofa ta fita, Mujaheed ya fara danna waya ya kai kunne sai kuma ya mike ya fita yana cewa hello, Imaan na shiga parlon ta nufi dakinta don har Daddy ya fita ganin bata ga motarsa a parking space ba, tana dauko kayanta ta ji an bude kofa, ta juya da sauri tana kallon kofar dakinta, can dai ta nufi kofar ta murda, Mujaheed ta gani tsaye kusa da kofar dakin nata, Xata gudu ya fixgota waje fuska daure yace "Ni dodonki ne kike gudu na?" Kuka ta fara yi a rikice taki yarda su hada ido tace "Ban son hka ni ka sake ni yaya" kallonta ya dinga yi kafin yace "Meyasa kike gudu idan kin gan ni" sosai xuciyarta ke bugawa tace "Ba komai, ni ka sake ni plss" ya sauke idonsa daga kallonta, can yace "What's wrong with you?" Da kyar tace "Ni na ji sauki" saketa yyi ya juya ya fita, ta durkushe wajen har sannan xuciyar ta bai daina bugawa ba. Da yammacin ranan Imaan na durkushe bakin tap din inna tana alwala kamar ance ta daga kai taga Sadeeq yana tahowa, da sauri ta rufe gashinta ta xaro ido, murmushi yyi, yana isowa inda take murya can kasa yace "Good evening dear, sae ynxu xa ki yi la'asar?" Bata iya tace masa komai ba ya tsaya bakin kofa yyi sallama cikin cool voice dinsa, Inna ta fito daki tana amsa sallaman, shiga yayi tace "Au, sannu da xuwa Bukar ashe kai ne" ya xauna yana murmushi yace "Ina yini kaka?" Tace "Lafiya lau Bukari, ya aiki?" Yace "Alhmdllh mun gode Allah" tace "Toh ya xafi xafi, ko da yake ma akwai Ac ko ina yanxu" Yayi dariya yace "Haka ne kaka" Tace "Toh madallah, bari in kawo maka ruwa da lemo" bata jira cewarsa ba ta debo masa su a fridge ta ajiye, tace "Toh nayi tuwo na ajiye maka ina bacci wannan mutumi Mujaheed ya shigo ya cinye" *The book Imaan is not free, you read for free ur cup of coffee*🤷🏻‍♀️ It's 300 via Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah Then u show ur evidence of payment via my WhatsApp digit 07087865788 to be included in the payment group.Sadeeq yyi murmushi yace "Wani lkcn ai sai ki min kaka..." Inna tace "Toh in sha Allahu kuwa, yanxu ya maganar da muka yi ranan Bukar?" Sadeeq yace "Kaka Abbana baya kasar ne, ina jiran sai ya dawo in sha Allah sai ayi magana" inna tace "Toh da kyau, Allah maido da shi lafiya, ai dama Bulasawa bai fiye xama ba aka ce, baya can baya nan, to abun ka da babban mutum fitattce..." yar dariya kawai Sadeeq yyi, sun fi minti talatin da inna dake ta basa labarin da ya kamata da wanda bai kamata ba, daga karshe ya ajiye mata dubu ashirin yyi mata sallama, xaro ido tayi tace "Kai dai baka gajiya Bukar, wancan ma da ka ban har yau basu kare ba wllh suna can na adana su sbda yaran gidan nan, toh ni dai nagode Allah ya maka albarka, ya kara maka budi" yana murmushi yace "Ameen kaka, nima nagode" inna tace "Toh ka gaida uwarka ka ji, wataran duk xamu san juna idan Allah ya yarda, to ya sunan uwar taka?" Yana murmushi yyi kasa da kai yace "Hajiya Khadijah..." Inna tace "Lahh sunan aminiyata a da kafin ta xama abun gudu, Allah sarki Hadiza ko ana wace duniyar yanxu kuma" Dariya kawai Sadeeq yyi yana kallonta, Inna tace "Allah ya sa mu yi kyakkyawan karshe dai, amma Hadiza bata yi abun kirki ba, ga son abun duniya Allah ya dora mata, wai..." Kofa ya nufa yana nurmushi yace "Sai na sake shigowa kaka" ta mike da sauri tace "Toh Bukar a gaida gida, Allah maka albarka" ya amsa da "Ameen" ya fita, Kalle kalle compound din kawai Sadeeq ke yi bayan ya fito amma har ya kusa gate bai ga alamar Imaan ba gashi wayar ta har sannan a kashe, mota ce ta shigo gidan driver yyi parking, aka bude motar umma ta sakko tare da Hajiya Balaraba suka bude bayan mota suka dinga fiddo manyan ledoji, Gaishesu Sadeeq yyi, Umma ta kallesa ta amsa tana ci gaba da fiddo ledojin, ya wuce su, sai da suka nufi entrance din shiga gida Hajiya Balaraba tace "waye wancan kuma" Umma tace "Kila wajen Yusuf ya xo" Hajiya Balaraba yace "Dama Yusuf na gari, ni na xata bai nan, duk na xo bana ganinsa" Umma ta tabe baki tace "Yana nan, kinsan sa bai fiye faram faram da mutane ba, ko yana gidan ma to idan bai dakinsa yana bangaren fitinanniyar kakarsu" Hajiya Balaraba tace "Shi yasa, amma na fi ganin Mujaheed" Umma tace "ko kwana hudu ba ayi ba aka gama wani case a gidan nan, wai Yusuf ya rasa warce xai fito yace yana so sai yar wajen Aisha" Hajiya Balaraba ta xaro ido tace "Yar wajen Aisha kuma, to sai aka yi yaya?" Umma tayi wani murmushi tace "Ai ba xancen ma yanxu haka, kakarsu dai tace ko bayan ranta bata amince da auren ba, kuma a ranan na shirya na je wani waje aka ce in kwantar da hankalina ba matarsa bace ba ma, wannan dai Hafsar ita ce matarsa kuma wai kwanan nan xa ayi bikin, kila a hada tare da na Mujaheed, tunda gashi har mun kusa gama hada lefen nasa" Hajiya Balaraba tace "Ke ma dai da daukan ma kai, to meye xaki wani damu a kan lamarin d'an kishiyar ki??" Umma tace "Ashe ma baki gama sani na ba kenan duk kusancin mu Balaraba, ni xan so abu mai kyau ya ra6a Aisha da 'yar ta, Yusuf ai abu ne mai matukar kyau, idan ya auri yar wajen Aisha ai ba karamin dace yarinyar tayi ba, ga arxiki ga shi da hankali da natsuwa, toh ina xan yarda, kiri kiri fa kun ga bakin cikin da ta dinga nunawa lkcn bikin Seeyama, babu abinda ta ta6uka da bikin sai dai ta leko ta koma, da aka tashi kai Seeyama ma ita ce karshen tafiya sannan farkon dawowa duk sbda hassada, shine xan yarda abun kirki ya sameta ita ma, inaa ai tunda naji ance min ba matarsa bace hankalina ya kwanta, sai ga kakarsu ma tace samm ba da yawunta ba" Hajiya Balaraba tace "Toh Alhmdllh" Hajiya Balaraba ta shiga jera tulin inner wears din da suka siyo kasuwa a daya daga akwatina takwas dake dakin Umma, Umma tace "Dole ma Mujaheed ya xo ya kara kudi, don wannan da ya rage ba isa xai yi ba don har gwal ina son mu saka a kayan, ko da dankunne da sarka da xobe ne kawai banda awarwaro" Hajiya Balaraba tace "Gaskiya kam, xa ma su fi ganin lefen da mutunci, to shi gogan na duba kayan ma kuwa?" Umma tace "Idan an gama hadawa sai su duba tare da ubansa, in sha Allahu kafin karshen watan nan xa a gama komai, su tafi su kai gaisuwa tare da sadaki da ubansa" Imaan na tsaye kitchen tana wanke plates a sink Ammi ta shigo tace "Kina da card a wayar ki in kira daddy nayi missing calls dinsa, mine is exhausted" Imaan ta juya ta kalleta da farko rasa abinda xata ce mata tayi, can a hankali tace "Ammi wayana baya wajena tun 3 days ago fa" Ammi na kallonta da mamaki tace "Baya wajen ki? To yana ina?" Imaan tace "Yaya ne ya amshe, ni kuma ban tambayesa ba har yau" Ammi ta wani hade rai tace "Wato ke baxa ki ji magana ta a gidan nan ba ko Imaan, ban raba ki da Mujaheed ba?" Imaan tace "Wllh Ammi ni na daina kulasa a gidan nan ki tambayi Inna, idan ma yaje part din inna ni shigewa daki nake ko in taho gida, wllh na daina xaunawa inda yake ma, kuma da ya amshi wayar ni ban tambayesa ba har ynxu, ban ma san wayar kuma ko ya bani" Ammi tace "Toh yayi kyau, xan ji ko shi ya siya maki wayar" Imaan tace "Wai don sbda Sadeeq na kirana fa shine ya karbe" shiru Ammi tayi tana kallonta, can tace "Toh ina ruwansa da kiran Sadeeq din?" Imaan ta bude hannu alamar bata sani ba, Ammi ta juya ta fice daga kitchen din. Da rana Aunty ta shigo parlon su Imaan da sallama, Imaan dake cin abinci parlor tace "Sannu da xuwa Aunty" Aunty tace "Yauwa Imaan, Ammi fa?" Imaan tace "Tana daki" direct bedroom din Ammi Aunty ta wuce, Ammi dake jera kayan guganta a press ta ajiye kayan hannunta tace "Yanxu nake son gamawa inje in maki ban gajiya Hajiya sai kuma ga ki" Aunty tace "Nima ban gajiya na xo maki ai" gaisawa suka yi Aunty ta xauna gefen gadon Ammi tace "Halan daddy ya koma" Ammi tace "Ehh tun jiya ya koma, ya su Maimoon fa, kwana biyu ni ban ga Yusuf ba ko tafiya yyi babu sallama" Anty ta tayi murmushi don har sannan tasan Ammi bata ji abinda Inna ta masa ba tace "Yana nan kuwa, amma next week xai tafi Abuja ina jin, aiki ne fa ya same mu in gaya maki..." Ammi ta xauna tace "Wani aikin kuma?" Aunty tayi yar dariya tace "D'an ki ne yyi min transfer daxu yana son mu fara hada masa lefe" Ammi tace "Yusuf?" Aunty tace "Ehh fa" Ammi tace "Ikon Allah, toh Allah ya bamu iko, Hafsar ce dai?" Aunty tace "Ehh ita" Ammi tayi dariya tace "Allah yayi kenan, kwanaki fa da nake tambayarsa ita ce min yyi shi fa ba ita xai aura ba, nace to wacece sai yace tana nan wataran xa mu santa" Aunty ta d'an yi murmushi tace "Toh dai jiya ce min yyi Hafsah" Ammi tace "Toh Allah yasa albarka, ya kuma sanya alkhairi" Sun d'an taba hira daga karshe Aunty tayi ma Ammi sallama, Ammi ta rakata har balcony tana ce mata sai ta leko ita ma. Tun daga wannan rana imaan ta fara wasar yar buyan gaske da Mujaheed, part din innan ma gaba daya bata son xuwa sai dole shi ma kai mata abinci, tana ajiye mata kuwa ko xaunawa bata yi xata juya ta bar wajen, Kwata kwata ita dai ba ta son ma su hadu, da ta tuna maganganun su Aunty Halima da Rabi'ah sai wani haushin sa ya diran mata, wai yana sonta, kai ta ma san kawai labarin su Anty Halima ne, ta ya yaya xai so ta, yanxu kam Sadeeq ta wayar Ammi yake kiranta dama da taji ring din wayar xata tafi da sauri ta duba ko shi ne, tun Ammi na complain har dai ta gaji ta daina. Yau da daddare Imaan na kwance parlor suna kallo tare da Ammi dake xaune aka danna bell, mikewa tayi ta sa Hijab ta nufi kofar ta bude, ido hudu suka yi da Mujaheed dake tsaye bakin kofar, gabanta ya fadi sosai tayi saurin juyawa ta basa hanya, ya shiga parlon yyi ma Ammi kallo daya ya sunkuyar da kai ya ajiye ledan hannunsa yace "Ina yini" tace "Lafiya lau, ya aiki" Yace "Alhmdllh, dama Abba ne yace in kawo wannan" Ammi tace "Toh Allah amfana" Yace "Ameen, sai da safe" Daga haka ya juya ya nufi kofa ya bude ya fita ya kulle kofar, Ammi ta bude ledan taga gasasshiyar kaza ce babba, duk son imaan da kaza kin ci tayi wai ta koshi, har hakan ya ba Ammi mamaki sosai, Ammi ta debi kadan ta kai sauran fridge ta ajiye. Ana saura few days su yi resuming schl ranan Friday da yamma sadeeq ya kira ta wayar Ammi, Imaan ta dau wayar da ke dakin ta yawanci, bayan sun gaisa yace mata yana waje, xaro ido tayi a hankali tace "Toh" daga haka ya katse wayar, Fitowa tayi daga dakinta gabanta na faduwa ta tafi dakin Ammi ta makale bakin kofa tana kallonta a hankali tace "Ammi ana kirana a waje" Ammi tace "Wa ke kiranki??" sunkuyar da kai tayi ta rasa wa xa tace don tun ranan da ta ambaci sunansa a gaban Ammi Ammi tace mata bata da kunya sunan Mahaifin nata take kira gatsau, to yanxu kam bata san ya xata kirasa ba, Ammi tace "Toh kar ki dade a waje" d'an murmushi tayi tace "Toh Ammi" daga haka ta fita dakin, as usual Hijab dinta har kasa ta saka ta fito, kamar mai tausayin kasa take tafiya har ta isa gate, Yana ganinta ya bude motar ya fito ya rungume hannayensa yana kallonta daga glass din idonsa, ta sunkuyar da kai har ta isa kusa da motar, cikin sanyayyan murya tace "Ina yini?" Yace "Lafiya lau dear, ya gida?" Tace "Alhmdllh" yace "Baki jin dadi ne, you look pale" tayi murmushi tace "A'a lafiyata lau" yace "To kaka fa, ko xa ki rakani in je in gaisheta" ta xaro ido tace "A'a ai bacci ma take" dariya yyi yace "Sure?" Tayi murmushi bata ce komai ba, yace "Ya Ammi" tace "Lafiyarta lau" yace "I want to take you out for shopping ko tare da cousin sisters din ki ne xata yarda?" Imaan ta xaro ido tace "A'a baxa a bar ni ba" yace "Ohk then" Shiru tayi bata ce komai ba shi ma haka, ta d'an daga kai suka hada ido, da sauri ta dauke kanta, murmushi yyi yace "On Monday xa ku yi resuming third term ss2, I am still counting fa" yar dariya tayi bata ce komai ba, yace "Yea, ss3 kuma term daya kawai xa ku yi shkkn, just few months to go in sha Allah" Imaan dai ba ta ce komai ba ta dinga kallon motar Mujaheed da yyi parking a nan waje maimakon ciki don har mai gadi xai bude gate sai kuma yaga yyi parking a waje, fitowa Mujaheed yyi daga motar kana ganinsa kasan daga asibiti yake, Imaan ta sunkuyar da kanta da sauri, Suna hada ido da Sadeeq har xai shiga gate sai kuma ya fasa ya nufe sa, Sadeeq yyi murmushi ya mika masa hannu hade da masa sallama, Mujaheed ya amsa yace "Ya aiki?" Sadeeq yace "Alhmdllh, wlcm back" d'an murmushi Mujaheed yyi ya juya ya nufi gate, sai bayan da ya shiga ciki Sadeeq na kallon Imaan da mamaki yace "Why didn't you greet him?" Tace "Ba ma shiri yanxu" ya buda ido yace "Why??" Tace "Nothing" Sadeeq yace "Uhn OK, nima daga hospital nake nace let me branch and see you pretty face" Tayi murmushi ta boye fuskarta, wani leda ya ciro ya mika mata, ganin bata ma san yana yi ba sbda fuskarta da ta rufe a hankali yace "Take dear" xame hannunta tayi ganin leda yake mika mata ta xaro ido tace "What?" Yana kallonta affectionately yace "Take plss" bata fuska tayi tace "Aa thank you bana so" yace "Karba plss" tace "Aa Ammina xata min fada" Shiru yyi yana kallonta, ta girgixa kai tace "Wllh Ammina xata min fada" Yace "Toh shikenan" cikin sanyin murya tace "Kayi hakuri" yyi murmushi yace "Na yi, kar Ammi tace kin dade, ki shiga ciki" tace "Toh nagode" Yace "No thanks dear, bari in shiga in gaida kaka" imaan ta xaro ido tace "Ae bata tashi ba" yace "Ehh xan tasheta" daga haka ya nufi cikin gidan ta bi sa da kallo, Inna na bakin tap ya sameta, ta mike tana washe baki tace "Allah sarki Bukari ka xo min gaisuwar juma'ah ne" yana murmushi yace "Ehh kaka" tace "Toh shiga ciki ka xauna, bari in dauraye wajen nan in shigo" yace "Toh kaka" shiga parlon yyi ya xauna, Inna ta gama dauraye daurayenta ta shigo tace "Toh ya mutan gidan Bukar?" Yace "Alhmdllh kaka, dama sauri nake, nace bari in shigo mu gaisa, ga wannan a ajiye ma imaan" ajiye ledan hannunsa yyi, Inna tace "Atoh bari in shiga da shi ciki, Allah yayi albarka" daga haka ta wuce ciki da ledan, sai ga ta ta dawo da bowl dauke da dambun nama, ta shiga kitchen ta dauko leda ta fito ta juye a ciki tace "Gashi nan jiya nayi ni kadai rai na wllh, ko yaran gidan ban tsamma ba ma" Yana murmushi yace "Toh nagode kaka" Imaan ta ajiye abincin hannunta tana kallon inna tace "Ina yini" mikewa inna tayi tace "Jira ni in dauko maki sakon ki, ni dai idan Bukar ya dawo xan ji ko Aisha ce ta hanaki xuwa bangarena yanxu, banda haka taya kina ajiye min abinci sai ki gudu kamar ana koranki, Aisha dai bata isa ta raba ni da ke ba tunda ba ita ta haifa min ubanki ba, idan ma ita ke hure maki kunne duk xan ji idan Bukar ya dawo, ni ba ruwana" imaan ta bi ta da kallo tana tabe baki, bata dau lkci a daki ba ta fito rike da ledan da Sadeeq ya bata tace "Wannan yaron kirkin ne ya xo daxu yace in baki, ko meye a ciki oho, kila wani zinarin ne ma, ni dai ban bude ba don ban gaji cin amana ba" Imaan ta xaro ido tana kallon ledan, can tace "Me yasa kika karba inna?" Inna ta hade rai tace "Toh baxan karba ba? A garin fulanawa kika ga ake maida hannun kyauta baya? Idan baki so sai ki bar min babu abinda ya sha min kai, ni ina so" wani kallo imaan ta mata ta bude ledan, still tayi tana kallon kwalin tsadadden waya da ake yayi, Inna ta saki wani kabbara tace "Toh idan ba Sadeeq din ba dama waye? Wa gare ki banda Allah sai shi din? Ko Bukar baxai siya maki dankareren waya haka ba balle Ahmadu" Imaan dai ta kasa cewa komai gabanta sai faduwa yake, Bude kofar parlon aka yi, Mujaheed ya shigo da sallama hannunsa rike da ledan fruit inna na washe baki tace "Mujaheed kalli wayar da yaron nan Sadeeq ya siya ma Imaan, ni nasan yayi dubu dari biyar" Mujaheed ya ajiye ledan hannunsa yana kallon kwalin wayar, Imaan ta mayar da wayar leda taki yarda ta kallesa ta mika ma Inna tace "Ki ajiye min" inna ta karbi ledan da sauri tace "Toh, nima dai na fiye surutu wllh" daga haka ta mike ta shige daki, Imaan ta mike ta fice daga parlon da sauri. Washegari asabar inna na daki ta ji an bude kofar parlornta ta fito tana tambayar waye, akwatuna taga ana shigowa da, ta saki baki tana kallon akwatunan tace "Meye wannan kuma?" *The book Imaan is not free, you read for free ur cup of coffee*🤷🏻‍♀️ It's 300 via Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah Then u show ur evidence of payment via my WhatsApp digit 07087865788 to be included in the payment group.Umma ce ta shigo parlon da sallama, su Ummi da Rahma da Maimoon suka xauna kan kujera Inna ta kalli Umma sannan ta kalli akwatunan tace "Lafiya Rukayya?" Umma ta xauna kan lallausan rug din parlon tace "Ina yini inna?" Inna tace "Cewa nayi meye wannan, daga ina??" Hajiya Balaraba da Hajiya Saude dake tsaye su ma sun shigo parlon suka gaisheta, Inna ta xauna kan kujera a fusace tace "Oh oh Allah, ni da ban yini ba xa ku gan ni, akwatunan meye wannan ake shigo min parlor dasu?" Hajiya Balaraba tace "Na lefe da xa a kai ne" Inna ta xaro ido tace "Lefen wa?" Hajiya Saude dake d'an tabe baki tace "Wacce Mujaheed xai aura..." Inna tace "Wani Mujaheed din?" Shiru duk suka yi basu bata amsa ba, Inna ta dinga sakin salati a jere, can tace "Yanxu Mujaheed aure xai yi ban sani ba sai dai inga akwatuna ana kokuwan shigo min da su ace min xa a kai lefe? Yanxu Rukayya mancewa kika yi ni na haifi Uban Mujaheed? Ehh lallai Ikon Allah ya fi gaban haka" daukar waya tayi ta mika ma Umma tace "Kira min d'an nawa.." Umma da ta daure fuska ta karbi wayar tayi dialing number Abba ta mika mata, Inna ta karba ta kai kunne, Abba na daga wa Inna tace "Yanxu Ahmadu ko ba raina kai ba mai ambatan sunana bane kace.... Allah sarki Inna, gashi Allah yayi lkcn auran Mujaheed baki a doron kasa balle ki sa albarka ke ma, Amma duk da haka muna maki fatan rahaman Allah... balle da raina da lafiyata Ahmadu?? wai sai dai inga katuwar matar ka na shigo min da jakunkuna tace min xa su kai lefe, yanxu ko shi Mujaheed din da nayi bauta da shi yana tsumma na cancanci yaki fadi min xa a kai lefensa sai dai inji a duniya? Wayyoo duniya Ina xa ki damu...." Bata jira cewar Abba ba ta katse wayar ta jefar kan kujera ta fashe da kuka tace "Oh oh Allah, duniya dai ba gaskiya, mutane basa jin tsoron Allah..." Hajiya Saude tace "Hajiya ba fa kai kayan xa ayi ba yanxu, kawai dai an gama hada kayan ne aka ce bari a xo a nuna maki, Amma ko gaisuwa ma ba a kai ga kai ma iyayen yarinyar ba tukun" Inna ta daga kai ta kalleta tace "Ai Rukayyar nan da kike gani ba mutum bace, idan uwarta ce Hadiza xata mata haka, Ina ce ranan da xa a fara hada kayan lefen ya kamata ta tako ta xo ta sameni tace to Inna gashi gashi, amma da yake xuciyarta ba tsoron Allah ban ganta ba, ni dai ba ruwana, kowa yyi da kyau.. kansa, bari kuma Ahmadun ya shigo in ji ko shi yace a boye min har sai an gama hada lefen" tana fadin haka ta Mike tana kakkabe kujerunta, mikewa Umma tayi tana kallon kawayenta da su Ummi tace "Ku kwasa mu je" Inna ta juyo da sauri tace "A kwashi me?? Ai ba ke kika min wahala da Mujaheed din ba, kuma da kyar idan ba da ni xa a kai lefen ba ma, don haka kada warce ta taba jakunkunan nan duk kuyi ta kanku ku fita ku bar min parlona in goge, nakudar Mujaheed kawai kika yi da haihuwarsa amma ni na masa abinda ya fi wannan, irin wahalar da nayi da shi ba sai dai Allah ya saka min ya biya ni ba, kuma shima Mujaheed din xai shigo ya sameni, idan bai ma yi hankali ba ma sai ince na bar sa da Allah..." tsayawa Umma tayi tana kallonta bacin rai karara fuskarta, tuni su Hajiya Saude suka fice a parlon, Ummi da su Maimoon suka bi bayanta, Inna ta juya tana kallon Umma tace "Ki fita don Allah xan goge daudar da ku ka shigo min da shi Rukayya" juyawa Umma tayi ta fice, Tsaye ta tadda kawayenta suna jiranta, Hajiya Saude tace "Amma gaskiya Hajiya Rukayya kina fama, yanxu haka kike xaune da wannan bala'eyyiyar tsohuwar nan har yau? Har yanxu kin rasa yanda xa ayi da ita ne?" Umma ta sauke wani ajiyar xuciya tace "Ku bari kawai, yanxu ina tanka ta abinda xata tsara ma d'an ta daban, shi kuma duk hakurinsa kika kuskura kika taba masa mahaifiya to babu xaman lafiya ranan, shi sa nake mata shiru" Hajiya Balaraba tace "Ke ma dai wllh, toh kin kasa yin komai a kanta ne?" Umma tace "So nawa kuma, sai dai Allah ya kyauta kawai, Amma wannan matar da ku ka gani ku kyaleta haka kawai" Hajiya Saude tace "A'a baki dai yi abinda ya dace bane, nima fa haka uwar mijina take a da amma ba yanxu ba kuma wllh, duk da nata bai kai na tsohuwar nan ba ma, Amma wllh ynxu sai labari, gaba daya gidan sai yanda nace ake yi, ina xan iya wahala??" Umma tace "Toh mu je ciki sai inji ya xa muyi, wllh na gaji, ita ce babban matsalata a gidan nan" Hajiya Balaraba tace "Toh kayan da ta hana fitowa da su fa?" Umma tace "Kayan xa su dawo hannuna in sha Allah, Mujaheed ne kadai ya isa ya fiddo da kayan daga parlon nan ko ubansa bai isa ba, kuma shi xan sa bari dai ya dawo" Hajiya Saude tace "Toh yaushe xa a tafi kai gaisuwar ne?" Umma tace "Uban cewa yyi sai kaninsa ya dawo Abuja, ae tuni na rufe bakinsa shi ma, komai nace cewa yake tohh" Duk suka kwashe da dariya suka shiga cikin gidan. Da magrib Imaan taje kai ma Inna abinci ta dinga kallon akwatunan da Inna ta jera a parlonta gwanin ban sha'awa, Inna ta shafe addu'an da take tace "In fiddo maki sabuwar wayar taki ne yanxu" Imaan tace "Inna wannan akwatunan fa?" Inna ta tabe baki tace "Daxu wannan mata Rukayya suka shigo da su wai ashe har xa a kai ma Mujaheed lefe bani da labari, Ina nan xaune kamar fanko" Imaan ta xaro ido tace "Aure xai yi Inna?" Inna tace "Ai shine nake jira Ahmadu ya dawo mu ji idan bola aka maida ni a gidan nan ban sani ba" Imaan da har sannan ke kallon akwatunan da surprise tace "Waow wllh sun yi kyau sosai, yanxu gidansu Aunty farida xa a kai kenan" Inna tace "Toh wacece dama banda ita, duk da dai iyayenta yaku bayi ne yarinyar na da hankali kuma ban jin xata gaji da ni idan na koma gidan Mujaheed da xama, lafiya xa mu xauna da yarinyar, ke kuma duk sati sai ki dinga xuwa kafin lkcn naki da bulasawa yayi" Imaan ta fara dariya ta xauna Inna tace "Toh bude mu ga tsiyar da suka xuba mata" Imaan na murmushi ta dinga sauko da akwatunan, sannan ta bude daya daga manyan ciki, xannuwa ne tsadaddu kwance a ciki, Imaan ta dinga fiddo su tana ajiyewa Inna na dauka tana duba kasan xannuwan don ganin ko babba ne ko karami, can ta tabe baki tace "Kin san Rukayya akwai shegen karya, ko sata xata iya sa Mujaheed yyi don tayi fafa, Toh xannuwa dai gasu duk masu tsada sai a xo a fidda min nawa da na takwarata a ciki" Imaan dai bata ce komai ba sai murmushi kawai take, ta bude wani akwatun, ta shiga fiddo laces masu suna lace, Inna ta rike ha6a tace "Ehh lallai Rukayya makaryaciya ce, wnn ai sai ta talauta min jika, Toh wannan ma sai a fidda min daya inyi doguwar riga, idan kyalle ya rage in baki a maki joni" Imaan dai bata ce komai ba ta bude akwatuna mai dauke da jallabiyoyi tsadaddu, Inna tace "Ki xabi wanda ya maki a ciki...." Imaan ta xaro ido tace "Innaa?" Inna ta hade rai tace "Toh sai su fidda min in baki" Akwatin dake dauke da takalma da jaka Inna ta bude, ta fiddo wani takalmi mai kyau sosai tana kallon imaan tace "Gwada wannan mu ga" imaan ta wani xaro ido a fusace Inna tace "Don Allah ki gwada" mikewa Imaan tayi xata sa takalmin aka bude kofar parlon Mujaheed ya shigo da sallama. Afuwan it's short, gobe da safe xan yi update in sha Allah, I was kinda busy gaba daya yau ne. Tnxx. Imaan isn't free, it's 300 via Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah.Kallonsu Mujaheed ya dinga yi, Imaan ta sunkuyar da kanta ta ki sa takalmin xata xauna, a fusace Inna tace "Ji walakanci don Allah, ba cewa nayi ki gwada ba?" Imaan ta hade rai tace "Toh nawa ne da xan gwada?" Inna tace "Oh oh Allah, yau naga fitina, to Ina ruwana da ko na waye, ni dai ba kawai in cire ma takwarata ba tunda ni baxan iya sa wa ba?? Ki gwada don Allah" Imaan dai bata ce mata komai ba ta xauna, Inna ta ajiye takalmin gefenta tana kallon Mujaheed dake tsaye tace "Toh da kaki gaya min xaka yi aure Mujaheed sai aka yi yaya? Sai aka dinga yagan naman jikina? Toh baxa dai a taba canxa ma tuwo suna ba, bauta dai na riga na gama maka sai dai Allah ya saka min da alkhairi, Amma kar dai ka manta akwai ranan sakamako" Mujaheed bai ce mata komai ba ya xauna kan kujera ya jinginar da kansa da kujerar a hankali yace "Akwai ruwan xafi?" Inna tace "Wanda Rukayya ta hado tare da akwatuna ta kawo min ba?" Mikewa Imaan tayi tace "Sai da safe Inna" Inna ta kalleta da sauri tace "Sai da safe bamu gama kallon kayan ba?" Imaan bata ce mata komai ba ta nufi kofa, Mujaheed ya bi ta da kallon gefen ido har ta fita sannan ya mike ya bi bayanta, Inna tayi tagumi tace "Naga abinda ya isheni ni patuu, wannan d'a na Ahmadu dai fitinanne ne, Ina lura da yarinyar nan gaba daya ta fita harkan ka a gidan nan, da ta ganka xata yi ta kanta ta bar wajen, gaba daya ta ma mayar da kai dodo, Ina kuma lura hakan na damunka ainun sbda baka samu damar dinga cutarta ba, to meye kuma xaka wani bi bayanta bayan bata kula ka ba, Ni dai gwara ma ayi auren nan ka kama gabanka jikata ta huta nima in huta da maganar ka haka, wllh ka cika fitina ko don maman Rukayya ka sha oho, tunda ita ma dai fitinanniyar ce" Juyawa Imaan tayi jin tafiya a bayanta, sosai gabanta ya fadi ganin shi ke bin ta, sai dai bata gudu ba sai kara saurin ta da tayi, ji tayi ya juyo ta har sai da ta kusa fadawa kansa ta fixge kanta gabanta na faduwa, a fusace tace "Meye haka yaya?" Kallonta ya tsaya yyi da wani expression, kamar xata yi kuka tace "Ni ka sakeni" Calmly yace "Me yasa kike gudu idan kin gan ni?" Kin cewa komai tayi, taji gaba daya she is very uncomfortable unlike before da bata ki ma ta fada jikinsa ba ta fara masa shagwaba, Yana kallonta yace "Imaan!" Kasa kallonsa tayi, ya dago kanta yana kallon manyan idanuwanta, turo baki tayi, and he couldn't stop looking at her, haka kawai yaji ya samu relieve din abubuwan da dama da ke damunsa, Yace "Answer my question now, me yasa kike gudu idan kin gani" sauke idonta tayi kasa calmly tace "Nothing..." jin shiru bai ce komai ba bayan few seconds ta daga kai ta kallesa taga kallonta yake, sauke idonsa yyi cikin cool voice dinsa yace "Saboda na amshi wayar ki?" Ta kallesa kafin tace komai ya ciro wayar a aljihu yana mika mata yace "Take..." bata san lkcn da tayi murmushi ba ta langwabar da kai tace "Ae daddy ya ce xai siya min wani soon" ya daure fuska yace "Take it now..." ta make kafada tace "Ni bana so kuma" yace "Take before I knock you" kamar xata yi kuka ta amsa yana kallonta yace "Shi kenan?" Tace "Ehh" wani boyayyen ajiyar xuciya ya sauke, ta d'an yi jim, sai kuma tace "Aunty Farida xa a kai ma kaya?" Kasa cewa komai yyi ya saketa ya juya ya koma part din Inna, ta bi sa da kallo kafin ta juya ta wuce part dinsu tana kallon wayarta. Mujaheed na komawa part din Inna ya tarar tana ta fiddo kayan akwatuna, ya xauna yana kallonta yace "Nima fa ban san an fara hada kayan lefen ba shi yasa ban gaya maki ba, sai daxu Umma ke nuna min" Inna tace "Ni dai ba ruwana, ku dinga jin tsoron Allah, don an gaya min ai ba gafara aka min ba...." Wani jallabiya mai kyau da tsada ta daga tana nuna masa tace "Wannan ai xai ma takwarata koh?" Kallonta ya dinga yi, jin yyi shiru ta ajiye gefe ta maida sauran ta rufe jakar, ta nuna masa takalmin da ta ba Imaan ta gwada tace "Wannan ma ai dai dai ita ne koh?" Nan ma dai bai ce komai ba ta ajiye gefenta, body spray biyu ta dauka ta ajiye gefenta tace "Sai ta dau daya ta bar min daya" murmushi Mujaheed yyi bai dai ce komai ba, Inna ta bude akwatin jewelries, ta dinga kallon dankunnaye da sarakuna masu kyau, kala biyu ta cire tana kallonsa tace "Wanne ya fi kyau cikin wa enannan?" Shi dai bai ce mata komai ba, ta ajiye biyun a gefenta tace "Sae ta xabi daya a mayar masu daya" bude pack din jan baki tayi ta cire uku tace "Duk da dai ba shafawa take ba sai ta ba Maimoon daya ta rike biyu" Kaf kayan sai da Inna ta bi ta cire daddaya ta ajiye ma Imaan sannan ta rufe jakunkunan ta jera su yanda suke, ta kwaso kayan ta xube su gaban Mujaheed tana kallonsa tace "Ko ban kyauta ba Mujaheed?" shi dai bai ce komai ba ta kwashi kayan ta kai daki ta fito tace "Toh ai faridan ma ya kamata ta xo ta gaisheni kafin a kai kayan, kwana biyu shiru bata xo ba" a hankali Mujaheed yace "Ba Farida xa a kai ma kayan ba..." Inna ta gwalo ido tace "Wa xa a kai ma?" Yace "Wata ce daban" Inna ta xauna kan kujera ta saki salati tana tafe hannu tace "Wayyoo.. Amma dai kai shahararren mayaudari ne Mujaheed, yanxu dama yaudarar yar mutane ka dinga yi ba aurenta xaka yi ba? Kasa yarinya ta kashe d'an kudinta ta siyo min turare duk da ba mai tsada bane, Mujaheed anya kana son wanyewa da duniya lafiya kuwa? Ina laifin yarinyar, kyakkyawa ce fa doguwa" Mujaheed dai kallon kasa kawai yake bai ce mata komai ba, ganin ynda ta dage tana kiransa da mayaudari ya dago ya kalleta yace "Umma ce bata son aurena da ita, shine ta hada ni da yar kawarta..." Inna ta xaro tace "Auzubillahi, yanxu Rukayya ce ta hanaka aurenta? Toh kuwa akwatunan nn babu inda xa su daga parlon nan sai gidansu Farida, yarinya mai hankali da natsuwa, tun da naga ynda take ji da Imaan take sonta naji nima ina sonta" Da sauri Mujaheed yace "A'a ita ma fa iyayenta sun riga da sun mata miji har an sa rana" Inna ta saki baki tana kallonsa, can tace "Toh wacece wannan kuma xa ka kwaso mana?" Ya d'an yi murmushin karfin hali yace "Idan anyi auren xaki ganta" Inna tace "Sai ka kawota ai ta gaisheni ba ruwana, Amma dai kun yaudara juna da farida tunda gashi ita ma har an mata miji kace, ohh mutane dai tsoron Allah yayi karanci a xukatansu, yanda ka taso gabana Mujaheed bai ci ace baka da tsoron Allah a xuciyarka ba, Toh ko da yake ai Rukayya ce ta haifeka, Ahmadu da na haifa ai gashi yana tsoron Allah, haka ma Bukar, duk basa yin abinda Allah ke fushi da, banda haka kayi ta xuwa gun yarinya kuna tadi ashe ba aurenta xaka yi ba??" Shi dai Mujaheed kallonta kawai yake, bude kofa aka yi Abba ya shigo, Inna ta tsuke fuska, Mujaheed kadai ya amsa sallamansa, Abba ya xauna yana kallonta yace "Ina yini" tace "Toh ni da aka ki gaya min xa a kai ma Mujaheed lefe sai aka yi yaya??" Abba ya girgixa kai yace "Kiyi hakuri, ni ma ba a gaya min da wuri ba Inna" Inna tace "Kai dai ka ajiye bala'i a gida kawai kuna xaune, banda haka ya xa ayi d'an ka a boye maka xa a hada masa lefe?" Mikewa Mujaheed yyi yana kallonta yace "Sai da safe" tace "Tou yaushe xa a kawo min yarinyar?" Yace "Ehh xa a kawota in sha Allah" daga haka yayi ma Abba sallama ya fita. Washegari Thursday Imaan na dawowa schl bayan ta yi wanka ta ci abinci ta shirya ta tafi part din Inna, Inna dake bakin pampo ta biyota ciki tace "Duk na cire maki kayan na boye maki a sif" Imaan ta xaro ido tace "Ni dai ba ruwana Inna" wani kallo Inna ta mata ta xauna kan kujera tace "Toh ni da ruwana, sai in ga wanda xai ce min don me" Imaan ta tabe baki ta xauna, inna tace "Daxu Bulasawa ya kirani muka gaisa, ni dai tunda uwata ta haifeni ban taba ganin yaro mai hankali da kirki irin yaron nan ba..." Imaan ta dai yi murmushi bata ce komai ba, Inna tace "Bayan mun gama waya ni dai nace masa iron dina ya lalace" Imaan ta xaro ido tace "Kika ce masa haka Inna?" Inna tace "Toh baxan ce ba, tun yaushe nake bin Bukar da Ahmadu su siya min sai su ce sun mance, dama wannan yaron isuhu kadai ne xan ce ma abu ya min nan take, shi Mujaheed ban ma sa shi a layi, ko ya siyo sai ya kai ma wancan katuwar matar, to wai ni isuhu na gidan nan ma kuwa?" Imaan ta bude hannu alamar bata sani ba, Inna tace "Ikon Allah ni toh bai xo ya ce min xai yi tafiya ba... Kai bari dai inje bangaren nasu inji lafiya, bai taba min irin haka ba da ma dai Mujaheed ne ni baxan damu ba" Inna ta saka Hijabi da ta dauko tace "Tashi ki rakani, ba lafiya yau kusan kwana goma ban ga isuhu ba, to ko bai da lafiya ne" Imaan ta mike suka fita parlon, Inna ta rufe kofar ta da makulli Imaan tace "Inna to meye na sa makulli" Inna tace "Baxan sa makulli ba? Ko datti ya shiga parlon ba a cuce ni, ko Kandangare ya ji shiru yana iya shiga in shiga uku" Imaan tayi gaba Inna ta bi bayanta tana cewa "Don Allah ki dinga cin abinci mai yawa Imaan, kinsan fa Bulasawa mai mutane ne, haka xa a ga amarya kamar tsinken tsire a sa mu a bakin duniya, ni dai ki rufa mana asiri" imaan dai bata tanka ta ba har suka iso part dinsu Maimoon, Inna ta shiga parlor tana kallon Ummi tace "Ke Isuhu na nan?" Bata jira cewarta ba ta wuce sama tana kallon stairs din palon tace "Matan Ahmadu dai kazamai ne, dubi fa yau basu goge nan ba ina ga" dakin Anty ta bude Aunty ta mike ganinta tace "Sannu da xuwa Inna" inna tace "Kwana biyu ban ga isuhu ba ko ke kika hanasa xuwa inda nake" Aunty tace "Ni na isa Inna, ban ma san bai je ba ai, yanxu dai baya nan" Inna tace "Toh yana dawowa kice ya xo ina nemansa" Aunty tace "Toh" Imaan ta gaida Aunty, Aunty ta amsa da fara'a, Umma ta leko ganin Inna ta koma ciki da sauri ta rufe kofarta, inna ta juyo tace "Toh ita kuma mai hada lefe ana ciki kenan, Toh dai baxan shiga ba" daga haka ta fara sauka stairs din Imaan ta bi bayanta. Bayan magrib Imaan na part din Inna Mujaheed ya shigo, xaunawa yyi ya gaida Inna da ke cin abinci tace "Mujaheed ni fa ban ga isuhu ba har yanxu, ban san me ya faru ba" Mujaheed na kallon boxes da ta jera yace "Inna xa a mayar da akwatunan can gida" Inna ta ajiye cokalin hannunta tace "A kan wani dalili?" Yace "Ai ba a gama xuba kaya ba" Inna tace "Toh sai a dinga xuwa nan ana xuba su, in dai kaga an fitar da akwatunan nan daga parlona to gidan amaryar xa mu tafi kai wa, ai ba wani ya min wahala da kai ba, ko Ahmadu da na haifa ban masa wahala yanda na maka ba, Rukayya dai ta shiga hankalinta a gidan nan ta daina shiga hurumin da ba nata ba" Bai kuma cewa komai ba, ya kalli Imaan dake xaune tana kallo, ta gefen ido ta ga yana kallonta ta mike tace "Sai da safe Inna" daga haka ta fita parlon, Bai dade xaune parlon Inna ba ya mike ya fita, yana isa part dinsu Imaan ya shiga balcony ya danna bell sannan ya bude kofar, Ammi dake xaune parlor ta dinga kallonsa har ya shigo, kasa kallonta yayi ya dukar da kansa ya xauna saman kujera yace "Ina yini Ammi" Ammi tace "Lafiya lau ya aiki" yace "Alhmdllh" tace "To maa sha Allah" kasa cewa komai yyi, can yana shafa kansa yace "Ammi dama..." Sai kuma bai ce komai ba, Ammi tace "Dama me?" Yace "Ina son Imaan xata rakani ne" Da mamaki Ammi tace "Ta raka ka ina?" Yanxu xan dinga update twice sbda xan rage tsayin rubutun, sai kuma da daddare in sha Allah. *The book Imaan isn't free, you read for free ur cup of coffee...*🤷🏻‍♀️ It's 300 via Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah, then you show ur evidence of payment through my WhatsApp digit 07087865788 to be included in d payment group. Mujaheed ya kalleta yace "Ina son xan je gidansu Farida ne" Ammi tace "Wace faridar? Wace ku ka yaudara ko wata daban?" Shiru yyi bai ce komai ba, Ammi ta tabe baki ta maida dubanta kan TV, yace "Ni ban yaudare ta ba Ammi, kila hakan Allah ya tsara we are not destined to be together" Ammi tace "Toh yayi kyau, haka Allah ya tsara" Bai ce komai ba, can ta kallesa tace "Toh me xaka je ka mata?" Yace "Ina son xuwa in bata hakuri ne, idan ta gan ni da Imaan she might listen to me, bana son tayi tunanin yaudararta nayi" Ammi tace "Toh Allah ya kyauta, amma yanxu dare yyi sai ka bari gobe" yace "Gobe da safe xata wuce kano" Ammi ta girgixa kai, tace "Toh ba sai ku tafi har da Maimoon ba" yace "Eh xa mu je tare" Ammi tace "To ka turo Maimoon din xa su fito tare" yace "Toh nagode" daga haka ya mike ya mata sallama ya fita parlon, Ammi ta mike ta shiga dakin Imaan xaune ta sameta tana karatu, Ammi tace "Ki shirya ke da Maimoon xa ku raka Mujaheed wajen Farida" Imaan ta xaro ido tace "Yaya kuma? A'a ni Ammi baxan je ba" Ammi ta dinga kallonta sannan tace "Me yasa?" Girgixa kai tayi tace "A'a ni bacci nake ji" Ammi tace "Me ya hada ku da Mujaheed din?" Da sauri ta kalli Ammi sai kuma ta dauke Kai tace "Ba komai fa Ammi" Ammi tace "Toh tashi ki rakasu ku dawo" daga haka Ammi ta fita dakin, da kyar Imaan ta mike har ranta bata son bin Mujaheed, can dai ta sa Hijab dinta har kasa ta fito, dai dai nan Maimoon ma ta shigo parlon, Ammi na kallon Imaan tace "You pray before leaving, and ku kula" A hankali Imaan tace "Toh" daga haka suka fita tare da Maimoon bayan ta gaida Ammi, a waje suka samesa yana jiransu cikin mota, Maimoon ta shiga back seat, Imaan ta hade rai ta shiga ita ma, Maimoon tace "Ki tafi gaba mana" Imaan tayi mata banxa ta rufe motar, Mujaheed yace "Wata ta dawo gaba, I am a driver to none of you" Maimoon ta turo baki ta bude motarta ta fita ta koma gaba, tada motar yyi suka dau hanyar titi, lkci lkci yake kallon Imaan dake kallon waje, gidan yayar Farida dake unguwar sanusi suka tafi, Mujaheed yyi parking kofar gidan ya kashe motar, yace "You two should go in, ku ce mata I am outside, she isn't picking her cals" Imaan ta bude motar ta fita, Maimoon ma ta fita suka shiga gidan a tare, A parlor suka tadda yayarta da yaranta uku, tana kallonsu ta amsa sallamarsu, Imaan ta xauna ta gaisheta Maimoon ma ta gaisheta duk ta amsa amma da alamar bata gane su ba ma, Maimoon tace "Aunty Farida fa?" Yayar tace "Tana daki" karamin yaronta ta aika ya kirata a daki, sai ga ta ta fito, tsaye tayi tana kallonsu, can tayi murmushi tace "Sannu ku da xuwa" Imaan tace "Ina yini Aunty farida" Farida ta xauna tace "Lafiya lau Imaan ya Ammi fa" Maimoon ma ta gaisheta ta amsa tace "Daga Ina ku ke haka da daren nan?" Imaan tace "Daga gida mana" Murmushin fuskarta yayi fading tace "Toh a xubo maku abinci" Imaan tace "A'a mun ci abinci, Aunty farida Ammi ce ta aiko ni" Farida tace "Ayya, toh ina jin ki" Imaan tayi murmushi tace "Ko xa mu je waje?" Farida ta mayar mata da murmushin sannan ta kalli yayarta tace "Anty kanin Mujaheed ne" lkci daya yayar ta hade rai ta ci gaba da kallonta, Imaan ta mike tayi ma yayar sallama Maimoon ma haka sannan suka fita, Farida ta mike ta bi bayansu, mamaki ya kamata ganin sun fita wajen gate don ta xaton cikin compound din Imaan xata bata sakon Ammi, ta dai bi bayansu har waje, sosai gabanta ya fadi ta tsaya tana kallon Mujaheed dake tsaye jikin mota ya rungume hannunsa, ta sunkuyar da kai ya karasa har inda take, Juyawa tayi xata koma ciki ya kamo hannunta a sanyaye yace "Pls listen to me Farida" kasa kallonsa tayi hawaye ya kawo idonta, sosai jikin Imaan yyi sanyi, Maimoon ta bude mota ta shiga don ita ma ta bata tausayi, cike da karfin hali Mujaheed yace "I neva meant to break ur heart Farida, even for once, but you know Allah plans best, may be we were neva destined to be together, ki yafe min pls, Umma ta bata son aurenmu and I can't disobey her" Hawaye na xuba idonta tace "Allah yasa hakan yafi alkhairi, and I am wishing a happy married life in advance" a sanyaye yace "Forgive me plss Farida" ta gyada masa kai da kyar tace "I have done that in sha Allah" Yace "Tun daga farkon relationship dinmu 4 years ago har xuwa yanxu idan na 6ata maki kiyi hakuri ki yafe min" tace "Baka min komai ba kuma na yafe maka ni ma ka yafe min, Allah kuma ya saka maka da alkhairi abubuwan da ka min from the beginning har xuwa yanxu, thank much Muhd, Allah kuma ya baka Ikon ci gaba da yi ma mahaifiyar ka biyayya, ku rabu lafiya" Ya sauke idonsa kasa yace "in sha Allah xa mu dinga xumunci..." xame hannunta tayi ta juya ta nufi gate dinsu, a hankali yace "Idan Allah ya kaddara you will still be my wife some days, I will be very glad in hada ki da kanwarki...." Farida bata juya ba har ta shiga ta rufe gate din, Juyawa Mujaheed yyi kamar mai tausayin kasa ya xaga ya bude driver seat ya shiga,Tada motar yyi yana kallon Imaan da ta turo baki bayan ta goge hawayen idonta, Bai ce komai ba ya bar layin da motar, har suka isa gida babu wanda yace komai cikin motar, the journey was very silent, yyi parking a kofar gida Maimoon ta bude motar ta fita, Imaan ma ta fita ta shiga gate da sauri, Parlor ta tadda Ammi, ganin mood dinta Ammi tace "Ya aka yi" xaunawa tayi hawaye ya kawo idonta tace "Ammi ta ban tausayi, me yasa Yaya xai mata haka, he betrayed her" Ammi ta tabe baki bata ce komai ba, tace "Har kuka fa sai da tayi" Ammi tace "Toh Allah ya bata wanda ya fi sa, wani hanin ga Allah bai wa ne, bata san ma wani gata Allah ya mata da ya rabasu ba, don Ina tausaya mata idan Mujaheed ya aureta barin yanda uwarsa bata sonta" Imaan tace "Toh Saboda me?" Wani murmushi Ammi tayi tace "Ko makiyina baxan ba shawara ya ba ma Mujaheed 'yar sa ba, Kinga Hajiya Rukayya ta wuce tunanin kowa, ni ba miji daya muke aure ba amma irin xaman da muka yi ba shi da banbanci da muna auren miji daya, na sha wahalar ta ne, sam bata san da annabi ya kafu ba" Imaan dai tayi shiru, Ammi tace "Don haka gwara dai ta aura ma d'an nata yar kawarta, sun fi kusa kuma sun san kansu" Washegari Juma'ah Imaan na dawowa schl ko uniform bata cire ba sai ga inna ta sha atamfarta mai tsada an yafa mayafi, Ammi tace "Sannu da xuwa Inna" Inna tace "Yauwa takwara ta dawo makaranta kuwa?" Ammi tace "Ehh yanxu ta shigo" inna tace "Toh da kyau, dama so nake ta rakani gidan ta rasulu kwana biyu shiru ban ganta ba" Ammi ta kwalo ma Imaan kira, Imaan ta fito, Ammi tace "Xa ki raka Inna anguwa" Imaan ta hade rai tace "Ban ma yi wanka ba kuma ban ci abinci ba, gashi kai na ma ciwo yake min" Inna tace "Kanki na ciwo kuma? Toh yi xaman ki bari in je in samu Maimoon ko Ummi su rakani, ya xan yi dake idan kin fadi a titi, wa gareni titin?" Daga haka ta juya ta fita, Imaan ta koma dakinta. Imaan na wanke wanke kitchen da yamma Ammi ta kwalo mata kira fito da sauri, Ammi tace "Kiran ki ake a waya" daukar wayar tayi ganin Sadeeq ne ta daga ta bar parlon, gaisawa suka yi yace "Pls dear ki d'an fito ki amshi sakon Inna am outside" Imaan tace "Sako kuma?" Yace "Ehh ko kina wani abu ne?" Tace "A'a ka dai shigo ka kai mata ai ni bn san da sakon ba" yayi murmushi yace "Ai anjima da daddare xan xo sai muje part din nata tare, yanxu sauri nake Mum dita ta aikeni xan kai mata sako" Imaan tace "Toh sakon meye?" Yace "Ke dai fito ki gani" a hankali tace "Toh" Daga haka ya katse wayar, Ammi dake jin wayar da take tace "Sakon meye?" Imaan tace "Ko ba Inna bace tace ya siya mata iron" tagumi Ammi tayi tana salati, can tace "Yanxu Inna mutunci take nema mana gun yaron nan ko tsiya, sam ban ji dadin sanin yaron nan da tayi ba, me kuma xata yi da iron idan ba fitina ba anjima ta hada kayan ta bada a goge mata gun masu laundry, wannan wani irin kaskanci ne fisabilillah, to ita Ina nata iron din?" Imaan tace "Daga ranan Ummi ta ce ya mata shocking shikenan Inna ta saka a bola" Ammi tayi salati tace "Wannan tsohuwa dai Allah ya raba mu da ita lafiya, ynxu abinda nake so da ke idan ta dawo anjima ki dau wayarta kiyi blocking number sa sannan kiyi deleting don ba mutunci take siya maki a gun sa ba, snn ki nuna masa baki son ma yana xuwa bangarenta kwata kwata" a hankali Imaan tace "Toh" Hijab kawai ta sa ta fita kofar gida, waya na kare kunnensa ya kafeta da ido har ta iso inda yake, katse wayar yyi yace "How are you doing dear" tace "Alhmdllh ya aiki?" Yace "Fine Alhmdllh" Bude motar yyi ya fiddo wani leda ya mika mata yace "Gashi ki ba Grandma" Shiru tayi bata ce komai ba, can ta amsa tace "Toh angode" wani ledan ya fiddo ya mika mata yace "This is for you" Ta girgixa kai tace "A'a nagode" a hankali yace "Bana son Ina baki abu kina ce min A'a dear" tace "Ni dai nagode" kallonta ya tsaya yi, dai dai nan mota yayi parking bayan nasa, Bude motar aka yi Umma ta fito, kallonsa ta dinga yi sannan ta kalli Imaan ta kara kallonsa ta kalli Imaan, Sadeeq ya gaisheta with respect, Sai da ya kara gaisheta ta amsa da sauri tace "Lafiya lau" Tana isa gate ta sake Juyawa ta kallesa saura kiris ta fada bakin gate din tayi maxa ta shige ciki, Sadeeq da ya bi ta da ido ya kalli Imaan dake wasa da fingers dinta yace "Who is she?" Imaan ta kallesa ta d'an yi murmushi tace "Mum din Yaya" Sadeeq yace "Ohk, but why didn't you greet her" Shiru tayi kamar baxata ce komai ba, can a hankali tace "Xan gaisheta ai idan na shiga" yace "Noo, that's not a point..." Ta d'an yi murmushi kawai, yace "Though I don't know why is that, and I am not suppose to intrude into family issue but promise me xaki dinga gaisheta daga yau, ita din ai babbace" Imaan ta kallesa, yace "Yea promise me" sunkuyar da kanta tayi a hankali tace "Toh in sha Allah" yayi cute smile dinsa yace "Maa sha Allah" kan wani farin kujerar roba ya ajiye ledan da ya bata ta ki ta amsa yace "Shikenan sai mu yi sadaka da shi tunda baki so, I am leaving now, mum dita na jirana" Bai jira cewarta ba ya shiga motarsa ya tada, d'an murmushi tayi cikin sanyayen murya tace "Toh nagode" ya kashe mata ido daya ya ja motar ya bar layin, a hankali ta kai hannu ta dau ledan ta wuce ciki. Sai kusan Isha ta tafi kai ma Inna abincinta bayan Ammi ta kara maimaita mata tayi blocking number Sadeeq a wayar Innan sannan tayi deleting, tana isa parlon ta ajiye abincin da ledan iron din ta gaida Inna dake goge gogen kayan kallo, Inna tace "Allah dai ya bar ni da ta rasulu kawai, Ni fa ta fiye min wasu daga yan uwa da basu da kirki ynxu, har maganar ki da yaron nan Sadeeq sae da na mata yanxu kawai kudi xan bada a kauda idon makiya a lamarin, gobe ma xan ba Mujaheed kudin ya kai mata, wa xai xauna yanxu?? Kowa ya tashi tsaye ya nemi kariya kawai" Imaan bata dai ce mata komai ba ta xauna ta dau wayarta dake kan kujera tace "Inna ga iron dinki an kawo daxu" Inna tace "Haba, Kai Allah masa albarka, to da Ahmadu ne sai dai yace min ya manta, kinga alamar wnn yasan darajan babba ko to ni dai ba ruwana, idan xaki rikesa hannu bibbiyu ki rikesa mijin aurena wllh, Allah dai ya saka masa da alkhairi, ke kuma na gaji da ajiyar wayar da ya kawo maki idan baxa kiyi amfani da shi ba a tafi kasuwa ki siyar kudin xai yi maki amfani" bata jira cewar Imaan ba ta shiga ciki, har Imaan ta gama blocking da deleting lambar Inna bata fito ba, tana kokarin tashi tace mata xata tafi, Inna ta fito duk ta hada xufa a gigice tace "La ila ha illallahu Muhammadur rasulillahi sallallahu alaihi wassalam, Innalillahi wa Inna ilaihi raji'una, laaa haula wala kuwata illa billahil Aliyul azeem... To barawo ya sace wayar" Imaan ta mike tana kallonta da mamaki, Inna ta fashe da matsanancin kuka tace "Wlh a karkashin kwalla na adana ledan wayar yanxu ko sama ko kasa wani ya shigo ya sace ban san waye ba, na shiga uku na lalace dukiyar mutane, Allah ka rufamin asiri" Mayafinta ta fixga ta fice daga parlon tana rusa kuka, Imaan dai tayi still tana kallon kofar dakinta can ta bi bayanta, tuni har Inna ta isa part din Abba, Imaan ta shiga nasu part din, Inna na shiga su Maimoon na gaisheta cikin kuka tace "Ina Ahmaduna yake?" Mujaheed dake sakkowa downstairs ya dinga kallonta da mamaki Aunty dake xaune parlor kuwa sai tambayarta me ya faru take, Inna ta rushe da sabon kuka ta xaune kasa tace "Nashiga uku, Ahmadun bai dawo bane?" Umma ta leko parlon daga kitchen bata dai fito gaba daya ba, Mujaheed ya karaso yace "Wai me ya faru ne??" Cikin kuka tace "An sace wayar da Bulasawa ya kawo ma Imaan a dakina cikin kwallaa...." Ta kunce ha6ar xaninta ta rufe fuska ta dinga kuka tace "Yanxu wani kallo yarinyar nan imaan xata min, wayar fa ance ya kai dubu dari biyar... Wayyo ni dai na shiga uku an goga min bakin fenti" Umma sai xaro ido take daga kofar kitchen tana kallon Inna jin ta ambaci Bulasawa, Aunty tayi tagumi tana kallon Inna, su Maimoon da Rahama kuwa banda dariya babu abinda suke kasa kasa. *imaan isn't free* it's 300 via Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah. Subscribe and read happily.Aunty tace "Daxu da kika fita baki kulle kofar bne Inna?" Inna na sharban kuka tace "Wllh na kulle Amina sai dai idan sabon makulli aka yi aka bude kofar..." Da mamaki Aunty tace "Ikon Allah, amma mu je dai a kara duba dakin Inna kila dai baki duba a nutse bane" a fusace Inna tace "oh oh Allah, Wani dakin xa aje kuma bayan nace maki duk na xaxxage kayan kwallan, wllh sacewa aka yi, kuma wannan barawon da ya san ni ne, yasan me nake ciki a rayuwa" Aunty na kokarin danne dariyarta tace "Gaskiya wannan abu da mamaki, anya ba Imaan din bace ta dauke kayanta kuwa??" Inna ta tsuke fuska tace "Don Allah Amina ki rabu da ni kiyi ta kanki, idan baxa ki fadi alkhairi ba kiyi hakuri ba don ni ba don Allah kiyi shiru, ta ina Imaan xata dauke waya bata gaya min ba" Tuni Mujaheed ya koma dinning ya xauna ya bude warmer yana diban abinci, Sallaman Abba yasa Inna ta mike tana matsar hawaye tace "Ahmadu yau an shafa min bakin fenti a gidan nan, ban san wanda ya shiga ya sace wayar da Bulasawa ya bani in ba Imaan ba, wayar tayi na miliyan Ahmadu, ka rufa min asiri mu tafi aje a sake dubawa, da wani idon xan kalli Bulasawa idan yaji labarin waya ya bata a wajena" Abba dake tsaye ya ma rasa abinda xai ce sai kallonta yake da mamaki, can dai ya girgixa kai yace "Wayar ta miye yaron ya kawo da ba mu da labari??" Inna ta wani hade rai tace "Ta imaan ce wayar ya kawo mata kyauta, kuma ta hannuna wayar ya biyo, ko an daina ihisani ne a duniyar?" Abba yace "Amma da ya bada ai sai ta kawo nan ta nuna min tunda shi Sadeeq bai nan, wannan bai kamata ba sam inna, a kan wani dalili ma xai bata waya??" Inna tace "Kaga Ahmadu kayi hakuri kar a shashantar da xancen bacewar waya mu tafi mu nemi waya duk inda ya shiga" Abba ya dinga kallonta, a fusace tace "Ahmadu kana kallona, don Allah ka shiga gaba mu je, idan ma ya kama a fiddo duk kayan cikin dakin sai a fiddo, yau dai xan ga batar nono a kirjin Budurwa" Kofa Abba ya nufa ta bi bayansa fuska a tsuke, Aunty ta fita ita ma, su Maimoon ma suka bi bayanta, Mujaheed dai cin abincin sa kawai yake a nutse, Umma da ta makale a kitchen, tana jin sun fita ta fito da sauri, duk ta hada xufa tace "Mujaheed, wani Bulasawan Inna ke nufi?" Mujaheed ya kalleta yana cin abincinsa a hankali yace "Ni ma ban gane xancen da take ba gaskiya" Umma ta tafi sama sai gata ta sauko da hijab xata tafi bangaren Inna, shi dai Mujaheed bin ta kawai yake da kallo har ta fita, Tana isa part din ta shiga parlon ta ga su Maimoon na ta fito da kaya daga cikin daki, Inna na tsaye daga gefe sai wurwurga ido take, Abba dai na tsaye daga bakin kofa ya rungume hannu, Aunty kuma na can uwar dakan Inna, Inna ta saki salati ta rushe da kuka tace "Kin ga ta kanki yau patuu, tunda uwata ta haifeni ba a ta6a ban ajiya ya bace ba..." Umma ta shigo parlon cike da damuwa tace "Wai har yanxu ba a ga wayar ba Inna?" Inna na goge hawaye tace "Wllh ba a gani ba Rukayya, ranan Ina bakin pampo ina gurje daudar wajen sai ga yaron ya shigo...." Umma tace "Wani yaro?" Inna tace "Bulasawa mana, waye bai san imaan da Bulasawa ba kuma a gidan nan, ba dai Bulasawan da kansa ba, d'an cikinsa ne dai, wllh yana bani wayar bayan ya fita kinga inda na ajiye wayar can" Umma ta kalli inda Inna ke nuna mata, Inna ta fashe da wani sabon kuka tace "Ni dai yau xan ga batar nono a kirjin budurwa ni Asabe" Umma dai ta kasa tsaye waje daya, Kai kana ganinta xaka ga tashin hankalin da ya ki boyuwa karara a fuskarta, Dakin Inna ta shiga ta gama xagaye xagayenta sannan ta fito tace "Kuma Inna babu kowa parlon San da aka baki wayar?" Inna ta d'an yi shiru sannan da sauri tace "D'an ki ne Mujaheed kadai a parlon a lkcn, Toh ga dankareren dankunnen zinari ma da ya bata ta bani ajiya bai bata ba, duk da ranan ba kowa a parlon ta bani, waya dai Mujaheed na wajen lkcn" Inna ta xaro ido ta dafe kirji tace "To ko dai sata Mujaheed ya fara a gidan nan ba a sani ba??" Umma dai sai hada xufa take tana kallon inna, Inna ta kalli Abba tace "Anya Ahmadu baxa a caji Mujaheed ba, wllh shine a parlon ranan, Ni dai na shiga uku na lalace" Abba dai bai ce mata komai ba, Umma ta dake tace "Inna bari in kashe gas na daura ruwan shayi, xan dawo yanxun nan, ae wannan babban magana ce" Inna tace "Yi maxa kar ki ja wata fitinar ba a gama kashe wata ba" da sauri Umma ta fita, tana komawa bangarensu bata ko kalli Mujaheed ba ta wuce sama jikinta na rawa. Washegari har Ammi ta gama soye soye a kitchen shiru imaan bata fito ba, dakinta Ammi ta shiga don ya ci ta fito ynxu ta gama shirin islamiyya, kwance Ammi ta ganta cikin duvet, ta cire duvet din tana kallonta ta kai hannu jikinta, janye hannun tayi tana kallonta tace "Imaan?" A hankali imaan ta bude idonta da ya rine tana kallon Ammi, Ammi ta xauna gefen gadon da damuwa tace "What's wrong imaan?" Da kyar ta nuna ma Ammi kanta murya can kasa tace "It's aching me" ta nuna ma Ammi kafafuwanta ma, Ammi ta dinga kallonta cike da tausayi tace "Kin daina shan maganin ki ko daughter!" Imaan ta girgixa mata kai kawai ta kasa cewa komai, mikewa Ammi tayi ta wuce bathroom dinta ta hada mata ruwan wanka ta fito ta daga ta, ita ta taimaka mata har xuwa bathroom din sannan ta fito, ta ciro mata kayan da xata saka sannan ta fita, Imaan na fitowa wanka ta kwanta kan gado daure da towel ta rufe jikinta da duvet, Ammi ta dawo dakin rike da cup din shayi da ledan bread ta ajiye kasa tana kallonta tace "Toh tashi ki shirya sai kiyi breakfast ki sha magani" Ganin she is shivering Ammi ta dauko cream dinta ta taimaka mata ta shafa sannan Imaan ta saka kayan da Ammi ta fiddo mata, shayi kawai ta sha da drugs dinta sannan ta kwanta Ammi ta fita da cup din. Aunty ce xaune parlon Abba bayan ta kawo masa breakfast, ganin mood dinsa tace "Don Allah ka daina damuwa da abubuwan inna, kun fa fi kowa sanin halinta, Bai kamata kuna sa abun a rai ba, kuma uwa ce fa" Abba ya girgixa kai yace "Ni kadai baxan iya dinga nuna ma Inna abinda ya dace da wanda bai dace ba, ya kamata ku ma ku dinga contributing...." Aunty ta sake baki tace "Mu a suwa Alhaji, ku ma ya ku ka kare balle mu, ai sai ta kora mu gidajen iyayenmu..." Abba yace "Wannan ba point bane, idan a nuna mata ta gyara ai da matsala babba, Dama ta fi sauraran Sadeeq to shi baya nan, ni kuma inyi magana ta fara min kuka, wllh duk abubuwa sun taru sun min yawa a kai" Aunty tace "Ai tana jin maganan Mujaheed ma" Abba ya kalleta yace "Toh cewa tayi a tafi Police station Mujaheed ne ya dauke waya, har da kukanta fa, Yanxu fisabilillahi maganan nan ya maki dadi?" Aunty ta kasa danne dariyarta tace "Tsufan kenan ai Alhaji, a dinga yi mata uxuri don Allah, Toh shi me Mujaheed din yace?" Abba ya girgixa kai yace "Ni ban ma gansa ba tun jiyan, sai daxu da muka hadu masallaci, gaskiya Inna na daga min hankali da yawa ban san yanda xan yi ba" Aunty tace "Toh Allah dai ya kyauta" Yusuf ne yyi sallama bakin kofa Aunty ta amsa ya shigo parlon ya mika mata wayarta yace "You missed a call" Abba na kallonsa yace "M.A fa?" Yusuf yace "Yana bedroom dinsa" Abba yace "Kira min shi ku taho tare" Yusuf ya amsa da to sannan ya nufi kofa, hanya ya ba Umma ta shigo parlon sannan ya fita, Daga Aunty har Abba suka dinga kallonta, duk gaba daya a sanyaye take tace "Alhaji xan je gidan Mariya wai suma ta dinga yi jiya basu yi bacci ba, yanxu haka suna asibiti tun asuba wai" Aunty tace "Subhanallahi, Toh Allah ya bata lafiya ya yaye ma duk musulmi ciwo, in sha Allah xan shigo anjima nima" da sauri Umma tace "A'a Hajiyar mu tace mu taho da ita zaria kawai, yanxu Ina xuwa Zaria xa mu wuce da ita" Abba yace "Toh Allah ya bata lafiya, ya sa kaffara ne" tana goge hawayen da ya cika idonta tace "Ameen" Abba yace "Da driver xa ku tafi kenan?" Umma tace "A'a adaidaita xan hau xuwa asibitin daga can sai mu tafi a motar mijinta" Abba yace "Toh Allah ya kiyaye hanya, do you need anything?" Tace "Ehh a min transfer din abinda ya sauwaka" Abba yace "Alright" sallama tayi masu ta fita parlon Aunty na mata Allah kiyaye hanya, bayan ta rufe kofa Aunty ta duba call din da tayi miss taga Ammi ce ta kirata, dialing number din tayi yana fara ring Ammi ta daga suka gaisa, Ammi tace "Dama tambaya xanyi ko driver na nan Hajiya..." Aunty tace "Ehh toh bai dawo daga kai su Maimoon islamiyya ba..." Ammi tace "Toh dama Imaan ce bata ji dadi ba xa mu je asibiti" Aunty tace "Subhanallahi tun yaushe?" Ammi tace "Yau dai da ciwon nata ta tashi" Aunty tace "Toh bari in ma Yusuf magana ko shi sai ya kai ku asibitin" daga haka ta katse wayar, Abba yace "Mamana ce ba lafiya?" Aunty tace "Wllh kuwa, Wai ciwonta ne ya tashi" Abba ya d'an yi shiru sannan yace "Bari Mujaheed ya shigo mu ji ko xa a kaita asibiti ne ko a bata medication a gida" dai dai nan Mujaheed ya shigo tare da Yusuf, Abba ya mike yace "Mu je ka duba Mamana wai bata ji dadi ba" Mujaheed ya d'an yi jim, sannan ya bi bayan Abba suka fita parlon, Aunty na kallon Yusuf tace "Kai baxa ka je dubata ba" Yace "Xan je anjima mum" Har bedroom din Imaan Abba da Mujaheed suka shiga Ammi dai ta tsaya daga bakin kofar, bacci take suka sameta, Mujaheed ya duka kusa da ita a hankali yana kallonta ya kai hannu forehead dinta, bude ido tayi ganinsa ta ja duvet ta rufe kafarta da sauri. Abba ya karasa kusa da gadon yace "Sannu mamana, ya jikin?" Da kyar tace "Da sauki Abba" Mujaheed na kallonta yace "Where are you feeling pains?" Ba tare da ta kallesa ba ta nuna masa kafafuwanta da baya, yace "Kin sha magani ne?" Kai ta gyada masa, Yace "Ina drugs din" ledan maganin dake ajiye ta nuna masa ya dauka ya duba su sannan ya ajiye yana kallon Abba yace "Let me get some injections da drugs" Abba yace "Ohk" daga haka ya nufi kofa Ammi ta basa hanya ya fita. Abba na kallon imaan yace "Allah ya sauwake imaan" ta d'an yi murmushi a hankali tace "Ameen" Abba ya juya ya nufi kofa yana kallon Ammi yace "Allah ya bata lafiya" Ammi tace "Ameen thumma Ameen" yace "Amma kada a gaya ma Inna" Ammi tace "In sha Allah" kofa ya nufa yace "Xan fita office, I will call later" Ammi tace "Allah ya kai mu, Allah kuma ya tsare" yace "Ameen" sannan ya fita parlon. Ammi ta karasa cikin dakin tana kallon imaan tace "In kara hada maki shayin ne?" Da sauri ta girgixa kai, Ammi ta dinga kallonta sannan ta juya xata fita, murya can kasa tace "Ammi don Allah ki shafa min maganin a kafa kafin Yaya ya dawo ni bana son ya shafa min" *Imaan isn't free....* it's 300 Via Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah Then you show ur evidence of payment via 07087865788 to be included in the payment group.... Mujaheed na dawowa ya tadda Ammi xaune parlor, Ammi ta amsa sallamansa yace "Ta ci abinci ai" Ammi tace "Ta sha shayi daxu" yace "Tana ciki har ynxu?" mikewa Ammi tayi tace "Ehh tana ciki" bedroom din Imaan ta nufa, ya bi ta da kallo sannan ya bi bayanta, Ammi ta cire duvet din jikinta xuwa kafanta tace "Imaan" tashi xaune imaan tayi ganin Mujaheed ta daure fuska ta ja duvet din xuwa waist dinta, a hankali tace "Ammi na ma fara jin sauki" Ammi ta kallesa tace "Magunguna ka siyo mata?" Mujaheed ya girgixa kai yace "A'a injections ne, sai na shafa..." Ammi tace "Ta sha drugs a bar injections din anjima" kallonta yake sannan yace "Amma na yanxu ne alluran..." Imaan tace "Toh na ji sauki ai yaya" Bai kuma cewa komai ba sai kallonta da yyi ta gefen ido babu yabo bbu fallasa, Ammi tace "Ina lotion din tube din?" Mika mata ledan yayi ta amsa ta cire man xafi dake ciki, Mujaheed ya kara kallon Imaan da ta ki kallonsa, Juyawa yayi ya nufi kofa kamar baxai ce komai ba bayan ya bude kofar yace "Sai anjima" ba tare da Ammi ta juya ba tace "Allah ya kai mu" da kanta ta shiga shafa mata man xafin a kafafuwanta da bayanta, Tana yarfe hannu tace "Toh Ammi alluran fa, ni dai bana son Yaya ya min, Kuma har yanxu Ina jin joint pain din" Ammi tace "Anjima Dr Habib xai xo..." Ammi na gama shafa mata ta fita dakin imaan ta koma ta kwanta ta lumshe ido. Da yamma Imaan na xaune parlor pepper soup din naman ragon da Aunty ta kawo mata na gabanta ta kasa ci don gaba daya bata da appetite, har wani rama tayi kamar warce tayi sati ba lafiya, xuwa lkcn dai ta ji sauki sai rashin kwarin jiki don Dr Habib ya xo ya mata injections din da Mujaheed ya siyo daxu, Ammi ce ta fito parlon ta iso kusa da ita tace "Idan baxa ki ci ba ki kai kitchen ki rufe Imaan, ai ba dole bane" Imaan bata ce komai ba ta amshi wayar da Ammi ke mika mata, Sadeeq ne ke kira a wayar, ta kalli Ammi da ta juya xata koma daki sannan ta daga wayar ta kai kunne hade da masa sallama murya can kasa, daga daya bangaren ya amsa yace "Are you okay?" Ta gyada masa kai tace "Sure Ina yini?" Yace "No, you sound sick ki gaya min baki da lafiya ne?" Cikin sanyin murya tace "Ae na ji sauki" Yace "Subhanallah, me ya sameki?" Ta girgixa kai tace "Kawai xaxxabi amma naji sauki sosai" ya d'an yi shiru sannan yace "Toh Allah ya kara lafiya, anjima xan xo in sha Allah" tace "Toh Allah ya kai mu" yace "Ameen, I will call you idan na iso" tace "Toh" katse wayar tayi ta ajiye tana shan pepper soup din naman a hankali, Bude kofar parlorn aka yi Inna ta shigo ta tsaya tana kallonta tace "Ikon Allah, yanxu don kaddara ta fada ma wayar ki sai ki kwanta ciwo imaan?? anya kuwa xa ki yi tawakalli irin nawa? Kinsan irin asaran da nayi a rayuwar nan kuwa tun tasowata har ixuwa yanxu? To 6arin ciki hudu nayi a gidan mijina, na haifi 'yan biyu suka mutu rana daya, dakina ya ta6a konewa kurmus bbu abinda aka fitar da sai mafici, kishiyata ta ta6a turo min yan fashi suka kwace min jakata a titi Allah ya so bbu komai ciki sai naira daya, 'ya yana uku kacal a duniya, da ubanki, sai na Mujaheed sai kanwarsu Hadiza dake kasashen turai, to ban gode ma Allah ba? Me ya sameni, ke don kawai an dauke wayar da bai fi dubu hamsin ba idan ma ya kai sai ki sa ma kanki damuwa kiyi ta ciwo kamar wayar jaraba, in dai waya ce ni baxan bari ki sani a bakin duniya ba xan ba Ahmadu dubu goma ya cika ya siyo maki wata ba ruwana" Imaan dai bata ko kalleta ba balle ta tanka ta, Ammi ta fito ta gaida Inna, Inna ta amsa tace "Aisha yanxu baki nuna ma yarinyar nan karatun tawakali??" Ammi tace "Ciwonta ne fa ya tashi Inna" Inna tayi shiru tana kallonta, can tace "Dama imaan na da wani ciwo ne da ban sani ba?" Ammi tace "Ciwon nata kuma Inna kika manta?" Inna ta rike ha6a baki Bude tana kallon Ammi, can tace "Ni dai ba ruwana, ku je kuna fadan haka wani ya ji, dama banda rashin lafiya da kowa ke yi Imaan na da wani ciwo na daban ne ban sani ba?" Ammi tace "Toh ko jiya ma Abbanta yace wannan yaron da ke nemanta ya kamata a sanar masa laluranta tun yanxu" Gwalo ido Inna tayi ta saki salati tana tafe hannu ta xauna ta rike kai tace "Naga abinda ya isheni ni patuuu, wayyoo Allah duniya ta lalace" dagowa tayi tana kallon Ammi tace "Aisha da hankalin ku ke da Bukar kuwa? Dama Imaan na da wani ciwo ne ni da ban sani ba, ku dai ku dinga fadin gaskiya ku ji tsoron Allah, yaushe rabon da in ji Imaan bata da lafiya a gidan nan, Ni dai kada wanda ya laka ma jikata ciwo lafiyarta lau, waye baya xaxxabin maleria da thypho, to kada ma ku kuskura wani yaji wannan mugun xancen, ku dai ba kwa fadan alkhairi a gidan nan, Ni dai ba ruwana, yaushe rabon da tayi ciwo?? Ai yafi shekara biyar ba ma banda sharri irin naku...." Mikewa Inna tayi ta nufi kofa rai bace tana cewa "Mutane dai ba tsoron Allah, meye kuma wai a gaya ma yaron da ke nemanta laluranta kamar mai cutar AIDS... Ni dai ba ruwana" a bude tabar masu kofar bayan ta fita ta kara gaba, Ammi na kallon Imaan tace "You make sure you tell him everything about ur health condition, kar ki boye masa komai" Imaan ta sauke idonta kasa a hankali tace "Toh Ammi" Ammi ta xauna kan kujera a ranta tana jinjina halin inna, imaan ta kalleta tace "Ya ce xai xo anjima" Ammi tace "Toh sai ki gaya masa" biyar da few minutes Sadeeq ya kira Imaan ta wayar Ammi ya sanar mata yana waje, bayan ta gaya ma Ammi, Ammi tace "Toh kar ki dade dai a waje" "Toh" kawai imaan tace ta sa hijab dinta ta fita, tana isowa gun motar ya bude mata back seat yana kallonta yace "Shiga ki xauna" girgixa kai tayi tace "A'a..." Yace "No pls ki shiga kinga you are sick, you look so weak, bana son musu get in plss" shiru tayi bata ce komai ba, komawa gefe yyi ta shiga motar a hankali, yana kallonta yace "Kun je clinic kuwa?" Tace "A'a Dr dina ya xo ya min allura" ido ya kafeta da shi, hakan yasa ta sunkuyar da kanta yace "What's wrong with you?" Ba tare da ta dago ba tace "I woke up with headache, backache and joint pain... pains everywhere...." Ya d'an bude ido da mamaki ya cire glasses din idonsa yace "Yana maki haka ne dama?" Ta kallesa ta gyada masa kai gently, kasa daina kallonta yayi, murya can kasa yace "Are you... A sickler?" Girgixa masa kai tayi tana murmushin karfin hali tace "I am a carrier, I am carrying the trait" jin yyi shiru ta daga kai ta kallesa, tausayi taga karara a kwayar idanuwansa yana kallonta, underneath his breath yace "Ya Salam, a very rare case, Subhanallah" murmushi kawai tayi bata ce komai ba, jingina yyi da motar ya rungume hannunsa yana kallon gate din shiga gidan looking so disturbed. Umma ta share xufar da ke keto mata bayan ta gama sauraran bayanin mutumin gabanta, Hajiya Saude sai jinjina kai take, da kyar Umma na gyara xama tace "Toh malam yanxu meye abun yi.... A taimaka don Allah, wllh ji nake kamar xuciyata xata fashe, ko kuma in hadiye xuciyar, duk duniya bani da makiya da ya wuce yarinyar nan da uwarta, uwarta ta xalunce ni a rayuwa ta cuce ni, a dalilin uwarta na shiga gararin rayuwa malam ka taimakeni ko nawa ne ni xan biyaka wllh, Malam ka dubeni..." Mutumin dake xaune gabanta ya girgixa kai yace "Auren nan fa na gaya maki idan ba wani Ikon Allah ba sai an yi sa, mijinta ne d'an gidan attajirin babu tantama, sai dai kuma wani Ikon Allah, gashi nan na gani, gashi nagani har ranan bikin..." Hawaye ya kawo idon Umma tace "A dai duba malam a taimaka" Malam yace "Toh ga takarda sai ki rubuta abinda kike son ayi a ciki, amma fa banda kisa... don yarinyar na da tsawon rai haka ma Yaron sai dai kuma wani Ikon Allah, sannan kuma baxa a iya raba su ba.... yar ki kuma da kike son yaron ya fara nema kuma ba mijinta bane baxai taba yiwuwa ba, ba mijin yar ki bane yaron attajirin.... Sannan ina maki tuni surkarki a tsaye take kan yarinyar.... Tasirin aikinmu a kanta kamar ko da yaushe dai kalilan ne kema kin sani, Ki rubuta komai amma banda abubuwan da na lissafo maki a baya" Umma ta gyara xama tana share hawayen idonta ta amshi takardan da biro ta ajiye kasa ta fara rubutu..... *imaan isn't free* it's 300 via Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah Then you show ur evidence of payment via my WhatsApp number 07087865788Da daddare Imaan na kwance parlon Inna dake xuba wani garin magani a kindirmon dake cikin cup din gabanta, Maimoon ta shigo da sallama ta ajiye abincin hannunta ta gaida ta, Inna ta mika mata cup din tace "Mika ma waccan matar" Imaan ta juya masu baya da sauri tana turo baki, Inna ta kalli Maimoon tace "Kinga walakanci ko, wannan wace irin yarinya ce don Allah, ta san daga inda maganin nan ya fito?" Imaan tace "Ni nace maki na sha magani fa a gida, ya xa ayi in hada magani iri biyu" Inna ta ajiye spoon dina hannunta tayi tagumi tace "Oh waannan 'ya ta Bukar dai jarababbiya ce wllh, Toh meye da maganin da baxata sha ba? Ba daci, ba 6auri, ba hamami, ba galmi sai ma gyara mata bakin ta da xai yi, ta ji dadi kuma a jikinta, to ni dai ba ruwana gashi can uwar ki da ubanki sun fara laka maki ciwon da ba a san ki da shi ba ba a san kansa ba, wai dama idan lkcn gabatar da yaro ya kusa ba duk iccen da aka jika ma yaron aka basa sai ya amsa ya sha ba sbda a kauda ikon makiya, Ni dai ba ruwana Ina taimakon ki kina min wlknci, idan ta uwarki ce sai dai fa ki mutu ba abinda xata maki, shi kuma Bukar na can na neman na abinci a Habuja, to wa gare ki banda Allah sai ni din, to ni ba ruwana, ki tashi ki amshi maganin nan ki sha ni ba asararriya bace, uwata bata ce min jeki kya gani ba da xan dinga maki bauta baki gani, ko ubanki bai samu haka a guna ba" Maimoon ta ajiye cup din hannunta ganin imaan ta ki amsa tace "Inna ni dai xan je inci abinci" Inna tace "Toh idan kin gama ki dawo kema ga naku da su fitsararrun can Ummi, ba dai don halinsu ba, ya xanyi tunda ni na haifi Ahmadun" Maimoon dai bata ce komai ba xata fita sai ga Mujaheed ya shigo parlon, gaishesa Maimoon tayi ta fita, Inna tace "Mujaheed waya dai ko sama ko kasa, an dai rasa wanda ya sace, ni na ma fi xaton hauro kantangar aka yi, ai daga yanxu ni kaca ma xan dinga sawa in rufe kofar da kwado idan xan fita, Ina dalili? Ai ko ya daukan ma kansa fitinar duniya" Mujaheed ya gaisheta sannan yace "Za a xo daukan akwatunan nan" Inna ta kallesa sannan tace "Ita da ta turo ka ba sai ta xo ta kwasa ba in ga, Rukayya dai tayi hankali da ni ba ruwana.... Wannan yarinya kuma kayi mata magana ta rufa min asiri ta dau nonon nan ta sha ba sato kudin nake yi ba, dubu goma kenan cikin kofin a kwance ta rasulu ta sa aka amso min" Mujaheed bai ko kalli imaan ba yace "Kaya xa a karasa xubawa cikin akwatunan shi sa xa a dauka" Inna tace "Sai kuma ka yi ai, ko Ahmadu bai isa yace xa a dau akwatunan nan ba balle kai" Kallonta ya dinga yi fuska daure, can ya juya ya fita. Washegari da safe Mujaheed ya shigo parlon Abba da sallama ta dalilin kiransa da yayi a waya, Abba na kallonsa yace "Jikin Imaan ya matsanta mata, yanxu Hajiya Aisha ta kirani..." Mujaheed yace "Toh a tafi asibiti kawai" Abba yace "Toh xa ka kai ta ne?" Girgixa kai yyi yace "Zaria xan tafi Abba, kuma likitan ta na gari ai" kallonsa kawai Abba yayi bai ce komai ba, Mujaheed yace "Xan je in shirya yanxu" Abba yace "Ohk then" Juyawa yayi ya fita parlon. Sai kusan la'asar Ammi da Aunty suka dawo asibiti da Imaan, nan parlor Imaan ta kwanta Ammi ta shiga kitchen don girka mata light food ta ci, Imaan ta jawo wayar Ammi dake vibrate kusa da ita ta kalli screen din, Sadeeq ta ga ke kira, sai da ya kusa katsewa ta daga da kyar ta kai kunne tayi masa sallama, ya amsa yace "Kun dawo gida ne?" Tace "Um..." yace "Ohk before magrib xan kawo maki drug din, but I have to see wanda aka baki a asibiti" tace "Toh" yace "Allah ya kara lafiya" a hankali tace "Ameen" yace "Do you need anything" tace "A'a" yace "Sure?" Ta gyada kai kamar yana ganinta, yace "Ohk sai na xo" daga haka ya katse wayar. Karfe shidda saura Yusuf ya shigo parlon da sallama, Imaan na xaune bayan tayi wanka ta shirya tana cin farfesun kayan ciki da Ammi ta mata, xaunawa yyi ya sakar mata murmushi yace "Sannu, ya jikin?" Ta mayar masa murmushin tace "Da sauki ya Yusuf" yace "Toh Allah ya kara lafiya, Ammi fa?" Imaan tace "Ta shiga daki" Yace "Ohk, me xa a kawo maki na marasa lafiya" ta kallesa ta marairaice tace "Kawai awara nake son ci" ya d'an buda ido yace "Awara?" Ta gyada masa kai a hankali, yyi murmushi yace "Toh bari a nemo maki" mikewa yayi yace "Anjima xan taho maki da shi, ki gaida Ammi idan ta fito" tace "Toh" daga haka ya nufi kofa ya fita, ko minti biyar ba ayi da fitansa ba sai ga kiran Sadeeq, sanar mata yyi yana waje tace "Toh ka shigo" Sadeeq ya d'an buda ido yace "Ni fa Ina jin kunyar Ammi" Murmushi tayi tace "Ae tana daki" Yace "Uhn toh gani nan shigowa" ajiye wayar tayi bayan ta katse, ta mike ta wuce dakin Ammi ta sanar mata Sadeeq xai shigo, Ammi tace "Toh haka xaki tsaya babu hijab" ta girgixa kai tace "A'a xan dauko a daki yanxu" Ammi tace "Ohk" daga haka Imaan ta fita ta shiga dakinta ta dauko hijab ta sa ta dawo ta xauna xata rufe farfesun gabanta yayi sallama bakin kofa, ta kalli kofar ta amsa sallaman sa, ya shigo parlon, sunkuyar da kanta tayi ya xauna saman kujera ya ajiye ledan hannunsa a kasa yana kallonta yace "Sannu Imaan, ya jikin?" d'an murmushi tayi tace "Ina yini" yace "Lafiya lau, Ina drugs din da suka baki a asibiti" mikewa tayi ta nufi daki ya bi ta da ido, ta dawo rike da ledan drugs din, ajiye masa tayi a kusa da shi, sannan ta koma ta xauna, yayi murmushi ya dau ledan ya fiddo Magungunan yana dubawa, can ya mayar da su, ya dau karamin ledan da ya shigo da ya ciro drugs biyu yace "You can take this also ba komai, na rubuta prescription din a jiki" ta gyada masa kai ya ajiye maganin, ya ciro wani na tube yace "Wannan ma ki dinga shafawa a duk inda kike jin pain" Imaan tace "Toh..." Ya d'an bude ido murya can kasa yace "Ko in shafa maki dear?" Xaro ido tayi ta kallesa sai kuma ta boye fuskarta a kujera, murmushi kawai yake yana kallonta, ganin ta ki dagowa yace "Toh baki cinye pepper soup dinki ba" a hankali ta dago tace "Ko xaka ci ne?" Yayi murmushi yana shafa beard dinsa yace "Ai baki bani ba" daukan bowl din tayi ta kai gabansa ta ajiye, ya xaro ido yace "I am only joking" tace "Ae sai ka ci" yace "Plss ki dauke, wllh wasa nake maki I am okay" ta make kafada tace "Ai kace ban baka ba to gashi ynxu na baka" ya wani xaro ido yace "Kar Ammi ta fito ki dauka plss" cike da shagwaba tace "Sai ka ci" yace "Ohk ohk idan na ci xaki dauke" tana murmushi tace "Ehh" yace "Toh dago min" daukan bowl din tayi ta rike da hannu biyu ta durkusa gabansa tana kallonsa har sannan tana murmushi, ya lumshe ido ya bude ya dau spoon din ya dau nama guda daya yayi kamar xai bata a baki ta koma baya da sauri, bakinsa ya kai spoon din ya ci, ta wara ido tana kallonsa, ya lumshe ido yace "It's sweet" dariya ta fara yi kasa kasa tace "Ashe kai ma ka iya kwadayi" da sauri ya bude ido, ta koma ta xauna still tana dariya, murmushi yyi yace "Ai xan rama" ta buda masa hannuwanta tace "Ko dai ka rame" kallonta kawai yake affectionately, ta turo baki tace "Ni dai ka daina kallona haka" dauke idonsa yyi yana murmushi yace "Watarana xaki yi bayanin me yasa xan daina kallonki" bude kofar parlon aka yi duk suka juya, daddy ne ya shigo parlon da jakar laptop dinsa Mujaheed na bayansa rike da traveling bag dinsa, imaan ta wara ido ta mike da sauri tace "Daddy" murmushi ya sakar mata, tana son xuwa ta rungumesa amma ta kasa saboda Sadeeq, ta isa gabansa cike da farin ciki, a hankali tace "Sannu da dawowa Daddy, baka ce min yau xaka dawo ba" Daddy ya shafa kanta yace "I just decided to come back and check on you daughter, how are you feeling now" tace "Da sauki sosai Daddy, har na ci abinci ma" amsan ledan hannunsa tayi, ya karasa parlon yana kallon Sadeeq kamar yanda Mujaheed ma ke kallonsa, Daddy na murmushi yace "Sadeeq" Sadeeq yyi kasa da kai yace "Sannu da dawowa Abba" Daddy yace "Thanks son, ya aiki" Sadeeq yace "Alhmdllh" Daddy yace "Ya Mai jikin?" Sadeeq yace "Alhmdllh she's getting better" Daddy yace "Maa sha Allah" Kallon Mujaheed Sadeeq yayi yace "Barka da yamma...." Mujaheed yace "Thank you" Ajiye jakar hannunsa yayi yana kallon daddy yace "Allah huta gajiya Abba" Daddy yace "Ameen son" imaan dai ko kallonsa bata yi ba kamar yanda shi ma bai ko kalleta ba ya juya ya nufi kofa, Daddy ya wuce bedroom dinsa, mikewa Sadeeq yayi yana kallonta yace "Kin ga kunyar da naji" dariya imaan tayi tace "Kunyar me? Sadeeq na shafa kai a hankali yace "Kunyar Abba mana" Imaan tayi murmushi bata ce komai ba, yace "Ki gaida min da Ammi, let me get going now" a hankali imaan tace "Toh nagode, Allah ya tsare" yace "Ameen dear, Allah ya kara lafiya, and plss kar kiyi wasa da drugs din ki" Ta d'an yi murmushi tace "In sha Allah" yace "Toh baxa ki rakani ba" tace "Toh xan raka ka bakin kofa" yace "Noo bakin mota dai plss my dear" tace "Toh idan na fadi a hanya fa" yace "Sai in daga ki sweet" boye fuskarta tayi ya nufi kofa yana murmushi ta xaro ido tace "Ka manta ledan ka" ba tare da ya juyo ba yace "Na ki dai" shiru tayi tabi sa da ido sannan ta bi bayansa, kamar mai tausayin kasa ta isa kusa da shi don tsaye yyi yana jiranta, a jere suka dinga tafiyar yana kallonta ita ko ta ki yarda ta kallesa, Ni kam nace waow perfect couples they will make... Lol, A dai dai bangarensu Maimoon Umma ta fito ta nufi parking space kana ganinta kasan fita xata yi, Sadeeq ya kalleta yace "Ina yini" tace "Lafiya lau" Imaan tayi kasa da kai a hankali tace "Ina yini?" Banxa Umma tayi mata ta bude back seat xata shiga, Imaan dai bata kalleta ba suka fita tare da Sadeeq, ido hudu tayi da Mujaheed dake xaune gun Mai kiosk dake kusa da gate din su, Dauke kai tayi da sauri, Sadeeq bai ma lura da shi ba, ya isa gun motarsa tana biye da shi, Yana kallonta yace "Keep on greeting her xata amsa wataran, you will loose nothing don kina gaisheta...." murmushi kawai Imaan tayi, ya kafeta da manyan idanuwansa, murya can kasa yace "Plss ki dinga cin abinci da yawa sweet, kin rame fa" ta wara ido tace "A'a ni dai haka nake" kallonta kawai yake bai ce komai ba, ta sunkuyar da kai tana wasa da fingers dinta, underneath his breathe yace "I have always loved you from day 1 imaan..." kasa kallonsa tayi gabanta ya dinga faduwa, kamo hannunta yyi a hankali ya lumshe ido xai kai lips dinsa ta kwace hannun da sauri tana satan kallon inda Mujaheed yake, kallonsu taga yana yi, Sadeeq ya kalli inda ta kalla suka yi ido hudu da Mujaheed, dauke kai yyi a hankali yace "We will talk later dear" daga haka ya shiga motar ta juya ta nufi gate gabanta na faduwa tana satan kallon Mujaheed da ya bi ta da ido fuskarsa dauke da wani expression, rufe gate din tayi tana kara kallonsa sannan ta wuce part din su da sauri. Mujaheed na gama parking ya juya yana kallon ummansa dake Bayan motar sai danna waya take, ta daga kai da sauri tace "Au, har an kawo ashe" bude motar tayi bayan ta ajiye wayar tace "Ka jira ni ba dadewa xan yi ba" yace "Umma aiki nake son wucewa don Allah kar ki dade" tace "Na sani baxan dade ba Mujaheed" daga haka ta fito motar ta shiga gidan Hajiya Balaraba, ita kadai ce babban gidan duk kishiyoyinta dama ta rabasu da gida, Hajiya Balaraba dake parlor xaune tace "Daga Ina haka Hajiya Rukayya" Umma tace "Daga gida Ina son kai ma Hajiya Saude kudin da ta ranta min na ba mutumi, sannan ku dai xauna da shiri sati mai xuwa xa a kai lefe gidansu Safeenah" Hajiya Balaraba tace "Toh Allah dai ya kai mu lafiya, amma ya ku ka kare jiya ina ta son in kira ki ko inje gida in sameki" Umma ta tabe baki tace "ya dai sa in rubuta masa abinda nake so ya faru, na kuma rubuta yace min in sha Allahu an gama, abu ne mai matukar sauki.... Kar ki so ki ga irin farin cikin da nake wllh Hajiya, idan hakan ya faru ae har Aisha ta mutu baxata rabu da ciwon xuciya ba" Hajiya Balaraba ta xaro ido tace "Toh me kika rubuta halan?" Umma ta rike ha6a tace "Cewa yyi kar in gaya ma kowa, ki sha kurumin ki aminiya, komai xai fito fili xa ki gani" Hajiya Balaraba tace "Amma xa su yi auren kuwa" Umma tayi dariya tace "Ehh to yace yaga da auren, amma ban jin abinda xai faru xai sa ayi auren nan... Kinga bari inje na bar Mujaheed yana jirana a waje" sallama tayi mata ta fita tana murmushi. *imaan isn't free* the subscription is 300 via Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah Then u show ur evidence of payment via my WhatsApp number 07087865788Imaan na kitchen tana yanka ma Ammi pumpkin leaves ta ji an danna bell, barin ganyen tayi a chopping board ta dauraye hannunta ta fito, bedroom dinta ta shiga ta dauko hijab ta sa sannan ta nufi kofar ta bude, Mariya ta gani tsaye bakin kofar ta xaro ido tace "Mariya Ahmad" Mariya na murmushi tace "Am I not welcm?" Sai a sannan Imaan ta kara ganin mugun kamar da suke da Sadeeq har dimples din, ta kamo hannunta cike da murnar ganinta tace "Sosai ma besty, daga Ina kike haka? Come in plss" Mariya ta shiga parlon tace "Mumy ce ta aiko ni wancan layin dake gaba da naku shine nace let me branch and say hi, ni da yayanmu ne ma" Imaan ta wara ido tace "Wanne?" Mariya tace "Wannan da ya taba maido ki gida da kika xo gidanmu" Dariya kawai Imaan tayi bata ce komai, har yau kuma tana mamakin me yasa Mariya bata ta6a nuna mata ta san suna tare da Sadeeq ba, ko bata sani bane?? She still can't tell, Imaan tace "Toh xauna plss in kawo maki ruwa mana" Mariya ta xaro manyan idanuwanta tace "Ya Sadeeq xai wuce kenan ya bar ni, dama kawai shigowa nayi mu gaisa ai daga gida muke, am okay dear" Imaan tace "Toh shkkn nagode kuma naji dadi" Mariya tace "Mum fa?" Imaan tace "Taje kasuwa tare da mamansu Maimoon" Mariya tace "Toh ki gaishe min ita idan ta dawo, mu je ki rakani, baya son jira wllh" imaan na murmushi tace "Toh shikenan mu tafi in raka ki" a tare suka nufi gate bayan sun fito parlon, Mariya tace "Ya shirin Sauka fa?" Imaan tace "Ina ta yi" Mariya tace "Ae kam gashi lkci sai matsowa yake..." Imaan tayi murmushi bata ce komai ba har suka fita gate, ta dinga kallon lafiyayyen ride dinsa dake parke a waje ba wanda ya saba xuwa da shi wajenta ba, tun da suka fito Sadeeq ke kallonta ta cikin glasses din idonsa ko kiftawa babu, har suka iso kusa da motar ya sauke glass din motar yana kallonta murmushi dauke fuskarsa, imaan ta sunkuyar da kanta tana fidgeting fingers dinta tace "Ina yini?" Cikin cool voice dinsa yace "Lafiya lau" Mariyata kallesa tace "Yaya ka tuna ta? Frnd dita din nan..." Sadeeq yyi murmushi ya girgixa kai yace "Ni kuma sbda mantuwa na yyi yawa kullum sai anyi min introducing dinta koh?" Dariya Mariya tayi tace "Eh mana Yaya frnds dina kullum ba ganesu kake ba sai kace ka manta, to ita ma nasan ka manta ta" Ya shafa kansa yana kallon Imaan har sannan yana murmushin sa mai kyau yace "Ita ai baxan manta ta ba" Imaan dai bata yrda ta kallesa ba, Mariya ta juya ido tace "Toh ya sunanta?" Yar dariyarsa yyi mai kyau yace "Kin fini sanin sunanta ai" Mariya tace "Na kamaka a nan, you are just pretending amma ka mance ta yaya" Sadeeq ya daga kafada yace "Ohk then, let leave it that way, na manta" Mariya tace "Tohm gwara dai" kallon Imaan tayi tace "Bye frnd ki gaida mum idan ta dawo plss" Imaan tace "In sha Allah, nagode da ziyara" Sadeeq ya d'an kalleta yace "Toh kawar Mariya sai anjima" Imaan ta hararesa ta gefen ido ta wuce ciki da sauri, ya bi ta da kallo yana murmushi, Mariya ta rungume hannayenta tace "Hmmm Yaya wannan kallon fa?" Da sauri ya kalli step sis din tasa, sai kuma yyi murmushi yace "Kallon gate din gidan?" Dariya tayi sosai ta xaga ta shiga gaban motar ya tada motar ya bar layin. Mamaki Imaan ta dinga yi na me yasa Sadeeq ke boye ma yan gidansu gashi dai ajinsu daya da Mariya both islamiyya da Schl amma bai gaya mata ba, tabe baki tayi ta cire hijab dinta ta shiga kitchen ta ci gaba da aikin da take. Bayan ta gama duk abinda xata yi bayan la'asar ta wuce part din Inna don su Ammi basu dawo ba har sannan, Mujaheed ta tarar bakin tap yana alwala, tun da ya kalleta sau daya bai sake kallonta ba ya ci gaba da performing ablution dinsa, ta wucesa ta shiga parlon Inna, Inna ta mika mata abun kwashe sharan hannunta wanda ba komai ciki sai few dirt tace "Xubar min wannan a bola, dubi fa parlon kamar ba komai amma ji yanda datti suka cuceni suka makale, kamar na sani nace bari dai in share in gani, ilai kuwa ga shi har da guntun kasa, kila ma wannan mutumin ne ya shigo min da su, sam datti bai da masugunni a parlona gaskiya" amsa imaan tayi ta fita ta kakkabe abun kwashe sharan ta dawo, ta bi Mujaheed da kallo ganin wucewarsa yyi ta shiga parlon, Inna ta shimfida tabarma ta xauna tace "Ke ki ji ya xo min nan ya kwanta salon ya fara wannan xaxxabin nasa a ce a parlon Inna haka ya faru" Imaan ta xauna saman kujera tace "Ba shi da lafiya ne?" Inna tace "Wai daga anje an kai kudin gaisuwa shine har ya fara tunanin rabuwa da ni bai san tare xa mu tare a can gidan nasa ba" Imaan ta xaro ido tace "Shi yace maki haka?" Inna tace "To sai ya fada?? ko bai fada ba nasan hakan ne ma, ke kinsan shakuwar da Mujaheed yyi da ni kuwa? Nima har na fara jin xaxxabin xai rufe ni" Imaan tayi dariya tace "Yaushe aka kai gaisuwan?" Inna tace "Daxu da safe su Ahmadu da Bukar da Bala da abokan Ahmadun suka kai... jibi kuma xa mu je kai lefe ki shirya tare xa mu dake" Imaan ta xaro ido tace "Har da ke?" Inna ta saki baki tana kallonta tace "Oh oh Allah, ban gane har da ni ba, to dama su waye masu kai lefen idan ban da ni... Ni ana bani mamaki wllh haka Ahmadu da Bukar wai bai dace ba inyi xamana a gida, to a kan me? Ni fa nayi wahala da shi Mujaheed din, sannan ba shi da wata kaka da ta wuce ni a duniya, in har baxan je ba dama sai dai iyayen yarinyar so su dau lefen da kansu ba ruwana" Imaan dai bata ce komai ba, Inna ta mike ta shiga daki sai ga ta ta fito rike da wani takarda, tana kallon imaan tace "Duk cikin jikokina kece kadai xan ce tayi abu tayi, da kyar kiyi min musu, sauran kuwa dama baxa su yi ba, to wannan ba wani damu na yayi ba don kansu suke ma, ga wannan wanka xa ki yi da shi ni dama baxan ba su Ummi su xubar min dukiya ba ba ruwana ba sato kudin nake ba, ke kadai ma amsowa" Imaan ta turo baki tace "Meye shi din?" Inna tayi kasa da murya tace "Wllh garin magani ne, sai kamshi ma yake, ko uwarki kada ki gaya ma ba hankali gareta isasshe ba sai ta hanaki amfani da shi, ki xuba a cikin bokitinki ki tara ruwa bakin ki a leko ki yi ki fito kin ji takwarata" Imaan tace "Ni wllh kaikayi xai dinga min a jiki fa" cike da fada Inna tace "Yau naga jaraba sai kace warce xan ba karara? Meye kuma wani kaikaiyi ni patuu? Garin magani ne fa ba wani abu ba" Imaan ta hade rai tace "Toh bana so baxan yi ba" Inna tayi kasa da murya tace "Toh yi hakuri takwara, abinda ma idan kika yi yau kika yi gobe shkkn, wllh dubu goma kenan kar ki ja min asara ba ramin kudi gareni a dakina ba, ba komai sai tarkacen kwallaye da tsoffin akwatuna" imaan ta turo baki ta amsa tace "Toh wai na meye?" Inna tace "Kaikayi koma kan mashekiya" Imaan ta xaro ido tace "Meye hakan?" Inna tace "Duk wanda xai sa maki ido a duniyar nan idonsa xai tsiyaye tass barsa da jakar idon, idan kuma mugun abu xai maki to fa sai dai ya koma kansa ne ni ruwana, babu wanda ya san ta yanda Bukar ya sameki" Murmushi kawai Imaan tayi, Inna tace "Su Maimoon ma ga nasu can na ajiye masu ba don halinsu ba" Imaan tace "Toh" Inna tace "Ni kwana biyu banji Bulasawa ya kirani ba, ko dai lambar ta bace a wayana ne shi sa baya iya kirana" daukar wayar tayi ta mika ma imaan dake dariya tace "Ke duba min, ba halinsa bane rashin kiran duk kwana biyu kya ga ya kirani mun gaisa har in fada masa damuwata" imaan ta gama danne dannenta ta mayar mata wayar tace "Network ne ya dauke sai bayan sati daya xai dawo" Inna ta saki baki tace "Saboda me toh?" Imaan ta mike tace "Ae haka yake yi" daga haka ta fice parlon tace "Na tafi" Inna ta ajiye wayar tace "Toh Allah ya mana tsari da su masu wayan" Ranan Friday da yamma babu yanda Abba da Daddy basu yi da Inna kan cewar tayi hakuri ta bar yan uwan umma, Matan kawu Bala, Ammi da Aunty sai kanwar umma da kawayenta biyu su kai lefe gidansu Safeenah ba inna tace samm bata san xance ba da ita xa a kai kayan, Daddy dake ta kallonta yace "Yawanci ynxu fa iyaye maxa ne ma ke kai kayan ba mata ba Inna, ke me xaki je kiyi cikin yara don Allah" Inna ta masa wani kallo tace "Toh ko a baka kayan ka kai ne Bukar?" Daddy bai ce komai ba, Inna tace "Yau naga jaraba, to wai ina ruwan Bukar a maganan nan fisabilillahi, Wai xanje cikin yara, A'a gyambo ce ni karewar girma, kawai ayi ta laka ma mutum tsufa, ni din nawa nake gaba daya tukunna ma dai, kamar warce dai ta haifi duniya??" kawu Bala yyi kasa da murya yace "Hajiya Inna da dai kiyi hakuri ki bari su kai kawai, ke fa babba ce...." Inna ta dakatar da shi a fusace tace "Kai rabu da ni Balalau, Ina ruwanka?? Ka san da xamana a kaduna ko ka taba xuwa takanas ka gaisheni? Ko gantalallun matan ka ma ba turo su kake ba balle yaranka, yau da Hurera na da rai xaka mata haka, Allah dai ya mata Rahama ya gafarta mata bata min komai ba, lafiya muka xauna da ita...." Mikewa daddy yyi ya fice a parlon, Inna ta bi sa da kallo tace "Wannan Bukar din dai ba shi da kirki wato ga mahaukaciya na magana shine ya fita, Wai... Ai da Bukar ne ke xaune a kaduna wllh baxan sha ruwa a gidan nan ba, mulkata kawai xai dinga yi da bafillatanar nan da figaggiyar Yar su, Toh sae Allah ya rufa min asiri Ahmadu ne, kwata kwata Ahmadu dama bai son abinda xai ta6a ni a duniyar nan shi da yaransa, kaga inda ya fi Bukar kenan, to meye kuma daga magana dai ta fahimta xai kwashi jiki ya fita" murmushi kawai Abba ke yi da kawu Bala da yyi hamdala a xuciyarsa da ta katse tsigesan da tafara yi ta koma kan daddy, Abba yace "Toh shikenan dai Inna, Allah ya kiyaye hanya sai kun dawo" Inna tace "Toh dama mota daya xa a ware mana da imaan da kawata ta rasulu, tace min tana hanya" Abba ya buda ido da mamaki yana kallonta, kawu bala yace "Toh madallah Allah kawota lafiya" daga haka ya fita Abba ya bi bayansa, Kawu Bala na ta murmushi yace "Ayi ta hakuri Barrister tsufa ne" murmushi kawai Abba yyi yace "Ana ta yi, sai dai Allah ya kara mana hakurin" Kuka umma ta xauna kan gado ta dinga rusawa jin da Inna xa a je kai lefe tana kallon kawayenta tace "Babu abun kirki idan aka tafi da matar nan wllh, xuwa xata yi ta mana tonon asiri, tayi ta sakin xance a gidan" *The book Imaan isn't free* it's 300 Via Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah Then you show ur evidence of payment via my WhatsApp digit 07087865788 subscribe and read without been judge by ur conscience.Mujaheed dai na tsaye kitchen sae kallon Umma yake har ta kai aya, jin yyi shiru a fusace tace "Wae ba da Mujaheed nake magana bane??" Ya d'an shafa kai yace "Ina ji Umma, Toh ni ya xan mata, kinsan tunda tace sai taje, ba wanda ya isa hanata xuwa ne" Umma ta hade rai tace "Yanxu baxa ka samo dubara da xaka hana xuwan nata ba, wllh idan taje gidan nan tsaf xata iya sa su fasa baka mata, tun da uwata ta haifeni ban taba ganin mutum sakakka irin tsohuwar nan ba, ni dai duk yanda xa ka yi ka rufa min asiri kayi ka hanata xuwa Marafan nan don Allah, ga ta can bakin motoci tsaye sai nuna hali take" Mujaheed yyi murmushin karfin hali yace "Toh..." Juyawa Umma tayi ta fice daga kitchen din rai bace, Inna dai na tsaye an sha super da mayafi da yar jakarta sae xuba kamshi take, duk mutan wajen dama sun bar jikin motar an bar ta ita kadai barin kawayen Umma, ta aika Maimoon ya fi sau uku ta kira mata Imaan amma shiru, ganin Maimoon ta dawo for the 4th time Inna tace "Yau naga abinda ya isheni ni patuu, Ina Imaan din ta shiga ne wai??" Maimoon tace "Inna ni fa ban ganta ba" Part dinsu Imaan Inna ta nufa fuska daure tana cewa "Ni ai xan ganta idan naje" Daddy ne xaune parlorn yana operating laptop dinsa, ta shigo parlon ko sallama babu tana kallonsa tace "Bukar Ina Imaan ta shiga ne wai, ko bata san duk jama'ah sun taru ita ake jira bane?" Daddy ya kalleta yaci gaba da abinda yake yace "Tana daki...." Inna tace "Kaga walakanci ko, wllh tarbiyar 'yar ka kalilan ne Bukar, ce mata nayi fa ta shirya ta fito mu tafi amma don wlknci ta shanya ni a rana ina ta jiran fitowarta, gafara xata min ne ko menene haka??" Daddy ya kalleta yace "Ku je Ina wai?" A fusace Inna tace "Kai lefen mana, ko gwari nake maka" girgixa kai yayi yace "Don Allah ki bari Inna, me xata je yi gidan... cikin manya kuma, kai lefe dai tun daxu ana ta abu daya ya ki ci yaki cinyewa, Ni nace mata baxa ta je ba don babu sa'anta a masu kai kayan, kema kawai don kince sai kin je ne babu yanda muka iya..." Inna ta saki baki tana kallonsa, can tayi kasa da murya tace "Meye laifina don nace xanje kai kayan jikana da nayi wahala da tun yana tsumma, me yasa baka da fahimta d'an uwanka ya fi ka fahimta Bukar...." Sai kuma ta fara matsar kwalla tace "Toh ai shikenan sai in fasa xuwa a kira ta Rasulu ace tayi xamanta, ai ba aikin Allah bane kai lefen na hakura" Daddy yace "A'a ni bance kar ki je ba tun da kinyi niyya kiyi tafiyar ki amma Imaan baxata je ba gaskiya" Inna tace "A'a su tafi, haka kawai in bata maku rai kan tsinannen lefe, dama ai babu sa'a na a masu kai kayan sai ta Rasulu ita ma xan sa a kirata ince tayi xamanta kawai, ae gaskiya ku ka fada, duk wanda kuma ya rasa mai gaya masa gaskiya a duniya yyi asara, ni dai na hakura da in bata maku rai sbda kayan mutane" Daddy dai bai ce mata komai ba har ta fita, Ammi da har ta gama shiryawa ta fito daga daki tana kallon Daddy tace "Kai me ya kai ka yin haka yallabai, maimakon ka barta tayi tafiyarta tunda ta sa rai" Daddy yace "Gwara ana yi ai ana mata gyara, ba gashi yanxu tace ta fasa ba, Amma komai tace be it right or wrong sae barrister ya biye mata" Ammi dai bata sake cewa komai ba. Inna na xaune parlonta bayan Yan kai lefe sun tafi kai lefen, Umma kam kamar ta xuba ruwa kasa ta sha duk tunaninta Mujaheed ne yyi mata magana ta fasa xuwa farin ciki gunta ba a cewa komai sai murmushi take bayan an tafi kai kayan. Mujaheed ne ya shigo parlon Inna da sallama ta dalilin sawa da Innar tayi a kirasa a waya, ita kadai ce parlon xaune kan kujera fuskarta shabe shabe da hawaye har da majina, Kallonta Mujaheed ya dinga yi da mamaki yace "Mai ya faru kuma?" Ta rushe da sabon kuka tace "Babu abinda Bukar ya mance bai gaya min ba Mujaheed wai daga nace xan je kai kayanka don Allah ya albarkaci kayan, shine ya tsitstsige ni ya gaggaya min ba dadi, yayi ta min bala'i kamar xai ari baki wai xan je cikin yara tsofe tsofe da ni, inda Bukar yake shiga ba nan yake fita ba, yayi min tatasss...." Wani kukan ta kara fashewa da, Mujaheed ya xauna yana murmushi yace "Shine kike kuka?" Cikin rawar murya tace "Baxan yi kuka ba Mujaheed, Bukar ya lalace, yau har nuna min yayi bani da iko da figaggiyar 'yar nan tasa mai ciwace ciwace iri iri kamar warce ta kashe d'an mutum, Ni dai ba Ruwana ba haka Bukar dina yake ba da, duk Aisha ta lalata sa da halinsu na fulani, ta sa ya xama jarababbe ya xama fitinanne, ga bakar xuciya.... Ni dai ban tanka sa ba nayi shiru Ina ta kallonsa don gani nayi abun ba na lafiya bane, Ni Ahmadu baya min haka komai nace sai dai yace min to, kwata kwata bai son bacin raina, Bukar dai ya lalace kuma ni ba ruwana da shi da 'yar sa.... su je can su karata idan Bala ma xai tafi ni bin sa xan yi kawai, duk kwana biyu sai in dinga kiran Ahmadu muna gaisawa" Murmushi kawai Mujaheed yake yace "Kece fa baki fahimci daddy ba ba fada yake maki ba kawai dai gyara ne" Inna ta daga hannu sama tace "A'a wllh fada ya dinga min kamar xai ari baki, ni ba ruwana kar ka xo nan ka karesa.... lalacewa ne dai ta riga ta samesa, har ni xai bude baki yace ma babu inda yar sa xata bi ni" Sai kuma ta fara kuka tace "A karkashin akwati fa na fiddo kayan nan ko sa su ban taba yi ba gashi yanxu babu inda naje sai na wanke su kar su yi warin jiki, kasan mutum ba komai bane facce datti" Mujaheed ya tabe baki yace "Kiran kenan?" Tace "Eh wllh, na rasa wanda xan gaya ma ne na kira ka, gashi har naji sanyi, to wa gareni dama banda Allah sai kai din, sai kuma Ahmadu" mikewa yayi yace "Toh ki shirya sai in kai ki gidan nawa ki gani...." Tace "Gidan da xa mu xauna?" Ta gefen ido ya kalleta bai tanka ta ba ya fita tace "Toh ai kawai bari in fito tunda ban tu6e kayan ba...." Mujaheed na isa part din su Imaan ya shiga da sallama, har sannan Daddy na parlorn a xaune, ya xauna saman kujera ya gaishesa with respect, daddy ya amsa da murmushi yace "Ya gajiya" murmushi kawai Mujaheed yyi yace "Abba dama wai Inna ce..." Sai kuma yyi shiru yayi yar dariya yana kallon daddy, daddy yace "Kiran ka tayi kenan" Kai ya gyada masa, Daddy ya girgixa kai bai ce komai ba, nan Mujaheed ya fada masa duk yanda suka yi da ita, daddy murmushi kawai yake yace "Dama xan je yanxu in sameta" Mujaheed yace "Amma kuma xan fita da ita xuwa can gidan ta gani, xaka sameta yanxu ko sai mun dawo?" Daddy yace "Toh shikenan ku tafi kawai, anjima xan je idan kun dawo, Ku tafi tare da imaan din..." Mujaheed yace "Toh" Daddy ya kira Imaan dake dakinta, fitowa tayi parlor, ganin Mujaheed ta xaro ido ta koma da sauri ta dauko Hijab dinta tasa, shi dai Mujaheed dauke kansa kawai yyi, Bayan ta sake fitowa daddy yace "Ki shirya xa ku fita tare da Inna yanxu" a hankali tace "Toh" daga haka ta juya ta koma daki, Mujaheed ya mike yace "Toh sai mun dawo Abba" Daddy yace "Toh Allah ya tsare, thank you son" murmushi kawai yyi ya fita parlon. Back seat ya bude ma Inna ta shiga tana cewa "Allah dai ya shiryi Bukar, Ni dai inaga bakin cikin 'yar kazar da xa a ban in ci a can yake min, to ni kuwa wani irin nama ne ban ci ba a rayuwar nan, ni wllh ya ma fara bani tsoro, sam ba haka yake ba da, yasan wahalan da nayi da shi yana karami kuwa, kamar fa baxai yi rai ba mayu suka kama min shi, kasan lkcn yana da kyau tsantsaa ga shiga rai yanda dai kaga wannan figaggiyar yar tasa da ya haifa, haka nayi ta wahala in gaya maka Mujaheed, Ni ce can nice nan cikin kishiyoyi gantalallu lkcn Ahmadu na da shekara hudu shi kuma ba shi da aiki sai shegen kiriniya yyi ta kwaso min kayan bola...." Rufe motar Mujaheed yyi bayan ta shiga ya juya suka yi ido hudu da imaan dake tahowa sanye da hijab dinta har kasa hannunta rike da wayarta.... Ya dauke kai ya xaga ya bude driver seat ya shiga, Imaan ta bude back seat xata shiga ya juya ya jefa mata wani mugun kallo yace "Do I look like ur driver?" Turo baki tayi bata shiga ba kuma bata ce komai ba, Inna tace "Oh oh Allah, kaga jaraba ko Mujaheed, yanxu wa ya gayyatota nan, ba Uban cewa yayi kar ta bi ni ba, meye kuma ta wani xo mana nan salalo salalo" Imaan ta hade rai tana kallonta, Inna tace "Ni dai ba ruwana, ki shiga gaba ki xauna tunda ubanki ba son tarayyar mu yake ba, ni ki daina ma xuwa min sashina nunawa yake a fakaice wai ina koya maki bakin hali" Imaan taji kamar ta juya ta koma bangarensu amma sanin Daddy na parlor kuma kafin ta fito ta ce masa ita baxata bi su ba yayi insisting sai taje, tasan tana komawa yanxu fada xai mata yace ta koma, haka nan babu yanda ta iya ta shiga front seat din fuskarta a daure. Tafiyar kusan minti ashirin suka yi xuwa gidan Mujaheed dake Unguwan sarki, throughout journey din Inna bata yi shiru ba, Daga Mujaheed har Imaan babu mai ce mata komai, wayarta dake hannunta ya fara vibrate ta kalla taga Sadeeq ke kiranta, silencing wayar tayi gaba daya ta saci kallon Mujaheed suka hada ido don shi ma kallon nata yake a sace, da sauri ta dauke kai bata sake kallon gefenta ba, Mai gadin gidan ne ya bude gate ya shiga ciki da motar yyi parking a space din mota uku dake cikin babban compound din da ya kawatu da shuke shuke masu kyau da daukar hankali, Kashe motar yyi ya fito, Inna ma ta bude motar ta fito tana kallon babban duplex din tace "Lahhh, toh ai wannan ya ma fi na ubanka kyau da haduwa, kasan lkcn da ka kawoni ba a gama ginin gidan ba duk sai na raina gidan...." Imaan ta bude motar ta fito fuska daure, Inna na kallonta tana washe baki tace "Kema dai Allah yasa wanda Bulasawa xai saka ki ya fi wannan komai da komai...." Tana fadin haka ta bi bayan Mujaheed da ya nufi main entrance din gidan, imaan ta bi bayansu tana tabe baki, da makulli ya bude kofar shiga gidan inna ta riga sa shiga tana rafka uban sallama, the parlor was well furnished, babu abinda babu a ciki na xamani, Inna ta rike ha6a tana kallon Mujaheed tace "Mujaheed duk kai ka xuba wa enannan kayan a parlon nan, kar fa kaje bashi ya hau kanka mu shiga uku..." Bai tanka ta ba ya wuce sama ta bi bayansa da sauri, imaan ta kyabe baki ta dinga bin hadadden parlon da kallo, wani kofa da ta gani a parlon ta bude ta ga daki ne babba da bathroom a ciki, ta kara bude wani taga makeken well furnished kitchen sai dai babu kaya a ciki, ta karasa cikin kitchen din ta bude wani kofa dake ciki taga store ne na ajiye kayan abinci, sai kuma wani kofa da xai yi leading dinka xuwa bayan gidan, rufe store din tayi ta fito ta rufe kitchen din ma sannan ta wuce sama, dakuna hudu ne a jere amma da distance mai d'an dama tsakaninsu, sannan corridor din na da fadi da tsayi sosai, wani kofa ta bude taga daki ne da bathroom a ciki, babu komai dakin sai Ac da curtains sai fitilu, ta rufe ta bude wani taga irin wancan ne, kin bude Wanda taga alamar suna ciki tayi don muryar Inna kamar speaker a dakin, ta bude last door din dake corridor din, well furnished parlor madaidaici ta gani ta shiga tana kare ma hadadden parlon kallo, can ta bude wani kofa da ta gani a parlon taga bedroom ne, shiga ciki tayi ta rufe kofar tana kalle kalle ta karasa ta bude wani kofar taga bathroom babba, ta d'an tabe baki ta juya ta nufi kofa ta bude suka ci karo da Mujaheed, juya masa baya tayi da sauri tana xaro ido, taji kamar ta nutse a wajen, jin yana sa makulli a kofar ta juyo da sauri tana kallonsa.... *Imaan isn't for free* it's 300 via Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah Then u show ur evidence of payment via my WhatsApp number 07087865788Ja baya Imaan ta dinga yi ganin kallon da yake mata fuskarsa a daure, ta 6ata fuska kamar xata yi kuka, a hankali tace "Yaya fita fa xan yi...." Bai tanka ta ba kuma bai fasa bin ta ba tana komawa baya, ganin kiris ya rage ya risketa ta koma can kusa da window din dakin ta tsaya xuciyarta na bugawa tace "Wayyo ni dai ka kyaleni in fita, me na maka" dab da ita ya tsaya, xata durkusa ya dago ta yace "Training da Ammi ta maki kenan na ba ma namiji hannun ki yayi kissing a bakin mota kina washe baki koh?" Ta wani xaro ido tana kallonsa, tsawa ya mata yace "Baxa ki bani amsa ba sai na baki dirty slap?" Tsorata tayi ganin babu wasa fuskarsa, kamar xata fashe masa da kuka tace "Ni fa Yaya...." Fixgota yayi lkci daya idanuwansa suka canxa yace "Ke fa me?" Kasa cewa komai tayi, ta hadiye abu da kyar tace "Don Allah kayi hakuri, ni bani na basa hannun...." Bai jira ta karasa ba ya buge mata baki da karfi, Ta kai hannunta da sauri bakinta, lkci daya hawaye ya kawo idanuwanta, cikin husky voice yace "I am making you this promise... babu abinda xai hanani gaya ma Abban ki sooner or later...." ta wani gwalo ido a rikice tace "Don Allah Yaya kayi hakuri wllh ba da gangan yayi ba shi ma bai sani ba" Bai san lkcn da ya kara buge bakinta ba, tayi tsit hawaye na sauka idonta, yace "Wato ke yanxu kina ganin kin girma kin isa tadi da maxa, har wani rawan jiki kike ki fita idan ya xo, har da jan sa xuwa parlon ku ki ajiye masa nama a gaba Saboda kinga Inna na goya maki baya, to bari ki ji abinda baki sani ba, as far as I Muhammad is concerned babu aure tsakanin ki da mutumin nan, you had better stop wasting ur time and face ur study, kamar yanda na xa6a ma Seeyama miji ke ma haka da kai na xan xaba maki mijin da ya dace da ke, duk ki gama rawan kanki xaki sha mamaki na, wannan mutumin da kike gani is just here to spoil and use you, ba so na tsakani da Allah yake maki ba, ki bar ganin yana kashe maki kudi ki xata wai son Allah yake maki, lalata maki rayuwa xai yi which I will neva allow, and let me give you this warning....." Ita dai hawaye kawai take xuciyarta na bugawa tana kallonsa, "Daga yau kika sake tsayawa kusa da motarsa sai na kusa sumar da ke wllh, duk karyar da xai maki ya maki a waya ba sai ya sake xuwa kofar gida ba, idan kuwa ba haka ba a gaban daddyn ki xan xane ki sai dai duk abinda Inna xata yi tayi..." Kuka kawai imaan take bata ce masa komai ba, strictly yace "Am I clear?" Ta gyada masa kai da sauri, muryar Inna suka ji tana cewa "Naga abinda ya isheni ni patuu na 6ata a gidan Mujaheed" sai kuma ta kwalo masa kira, bude kofar Mujaheed yyi ya fita ya jawo kofar, Imaan ta durkushe a dakin tana kuka a hankali, Inna na ganin Mujaheed tace "Alhmdllh, ni na xata 6ata nayi, Toh ita kuma matar ina ta shiga, har kasa fa na sauka ban ganta ba, kada ta shiga wani waje in shiga uku dama ga Bukar ya xama abun tsoro, ba da xuciya daya ya yarda ta biyo mu ba" Mujaheed yace "Tana waje, muje ki ga dakin dake kasa" Inna tace "Na waye dakin?" Yace "Baki" inna tace "Irin su Hansai da 'ya yanta knn idan sun xo" murmushi yyi ya bude kofar parlon yace "Har ke ai" Bai jira cewarta ba ya fice. Har garden sai da Mujaheed ya kai Inna ya xaga duk gidan da ita, tana kallonsa tace "Toh ai tun yanxu ya kamata mu shiga gun makota a san juna kafin mu tare, ko ya kaga?" Kallonta yyi ya dauke kai, tace "A'a ba xancen dauke kai ba yana da kyau in san su su san ni, ko haka mutum xai ta xama ba jama'ah a gida, ai mutane Rahama ne" Mujaheed yace "Sai ki jira idan kin ga dawowarki gidan" Inna tace "Wannan gaskiya ne, to ni na shiga uku ban fa yi la'asar ba Mujaheed" yace "Toh mu je ciki kiyi" parlon suka koma ya nuna mata dakin dake downstairs yace "Sai kiyi alwala a bayin ciki kiyi sllhn" tace "Toh dakin su Hansai kenan" shi dai bai ce mata komai ba ta wuce ciki, kallon agogo yyi sannan ya wuce sama, parlonsa ya shiga ya bude kofar dakin, durkushe ya ganta inda ya bar ta har sannan tana kuka, tana ganinsa ta mike tsaye, karasawa cikin dakin yyi, ta hadiye kukan da take ta sunkuyar da kanta, takawa yayi har gabanta ya tsaya ta ki yarda ta daga kai balle ta kallesa, ya dago kanta a hankali, ta kallesa sai kuma ta fashe da kuka ta juya masa baya, xagawa yayi gabanta ta rufe fuskarta tana shessheka, d'an murmushi yyi, kamar baxai ce komai ba sai kuma yace "ki dinga jin magana ta idan baki son na dinga sa ki kuka" ta kara juya masa baya cikin kuka tace "Ni bana soo" xagawa ya kara yi gabanta ya jawo ta kusa da shi, ta kuma fashewa da kuka, ya d'an hade rai yace "Toh baxa ki yi shiru ba" kin cewa komai tayi, ya ja ta xuwa bathroom, ruwa ya bude yana kallonta ta madubi a hankali yace "Wash ur face now" ta turo baki ta ki cewa komai, tara hannunsa yayi ya debi ruwan ya dukar da ita ya shiga wanke mata fuskar, yana gamawa ya ciro handkerchief dake aljihunsa ya fara goge mata ruwan fuskar, yana kallonta ta madubi yace "Promise me xaki fara jin magana ta daga yanxu...." Kin cewa komai tayi ya hade rai yace "I am talking to you" da kyar tace "Na ji" yace "Kin ji me?" A hankali tace "Abinda ka ce" mayar da handkerchief din yyi aljihunsa ya juya ya fita bathroom din, murguda baki tayi ta juya tana kallon kofar bayin. Parlor Mujaheed ya xauna yana danna wayarsa har Inna ta fito dakin da ta shiga yin sllh, tace "Wai Mujaheed ni fa ban ji motsin Imaan ba.... A rufa min asiri mu dubota" Mujaheed yace "Tana sama ai" Inna tace "Toh ni dai mu je in ganta" bata jira cewarsa ba ta nufi stairs ya mike ya bi bayanta, dakinsa ya shiga da ita suka ganta tsaye jikin window waya kare a kunnenta, tana jin an bude kofa tayi saurin dauke wayar daga kunnenta tayi tsuru tsuru, kallonta Mujaheed ya dinga yi, Inna tace "Toh ke daga ganin gida sai ki shige dakin matar mutane ki xauna, jira xa ki yi Allah ya kawo lkcn naki da Bulasawa ae" Juyawa Mujaheed yyi ya bar bakin kofar, Inna tace "Toh fito masu a daki yi hakuri haka" imaan bata tanka ta ba ta nufi kofa gabanta na faduwa ta fita, Inna ta bi bayanta, balcony suka tadda Mujaheed suna fitowa ya kulle gidan da makulli ya tafi gun motarsa, imaan bata yrda ta kallesa ba ta bude front seat ta shiga kamar munafuka Bayan Inna ta shiga baya, ya ja motar ya fita compound din yyi ma Mai gadi sallama. Suna hawa saman titi Inna tace "Ni dai Mujaheed da dai in samu kaza in siya, naji raina na so sosai" Mujaheed yayi parking dai dai gun masu gashin kazan da ta gani ya sa tayi magana, tana washe baki tace "Allah dai ya maka albarka" Bai ce komai ba sai ma jinginar da kai da yayi da kujeran motar ya lumshe ido, Inna tace "Toh ko ta fita ta amso?" Ba tare da ya bude idon ba yace "Ehh" inna tace "Toh guda nawa?" Jin bai ce komai ba Inna ta gyara xama tace "Ko guda uku ai yyi, Ni daya ita daya, yan sa ido kuma sai in kacalcala masu daya" Mujaheed yace "Ohkk" Inna tace "Yi maxa ki sauka imaan, kice masu su xabo manya don Allah na tsohuwa ce kuma ba miji gareni ba" Imaan ta bata fuska ta juya tana kallon Inna, inna tace "Naga Ikon Allah, ko in sauka da kaina ne? Me mutanen xa su maki ko ina ruwanki da su" bude motar Imaan tayi ta fita ta tafi gun masu gashin, Mujaheed ya bude ido ya bi ta da kallo daga cikin motar, ba laifi akwai maxa a gun, imaan na sunkuyar da kai ta amsa tambayar da masu wajen ke mata tace "Guda uku" tana ta tsaye har aka gama packaging kajin a leda daban daban ta amsa ta nufi gun mota ta bude back seat tana kallon Inna tace "Wai dubu hudu da dari biyar" Inna tace "Toh ni xa ki gaya ma? sai ki gaya ma me siyan ai" Ta madubi Mujaheed ya kalleta yace "Waye me siyan ban da ke?" Inna ta gwalo ido tace "Ban gane ba" ya buda ido sosai yace "Ko sisi bani da shi, ban fito da kudi ba" Inna ta saki salati mai tsayi tana xaro ido tace "Nima ko sile ban fito da ba Mujaheed" Mujaheed ya daga kafada yace "Sai ki san abinda xaki ce masu" Inna ta kara sakin salati tace "Yau babu lafiya ni patuu an kacalcala kaji uku ba kudi" shi dai Mujaheed bai sake ce mata komai ba, ta kalli Imaan da xaro ido tana kallonsu, Inna tace "Maxa maida masu tsiyar su kice basu da girma an fasa siya, maxa koma" Imaan ta wani xaro ido tace "Iyyee, bayan an yanyanka wllh ni ba inda xan je" a fusace Inna tace "Da aka yanka ci muka yi? Ni naga abinda ya isheni, ki juya ki mayar masu kayansu ba mu da halin biya" Imaan duk ta rikice barin yanda taga duk mutan wajen na kallonsu tace "Na shiga uku, wllh Inna baxan iya komawa dubi fa maxa a wajen da yawa" jaraba Inna ta dinga yi inda take shiga ba nan take fita ba tace "Mazan banxa maxan hofi ina ruwanmu da su bamu da kudin biyan kaji..." wani gentleman dake xaune wajen ne ya taso ya iso gun motar yana kallon Imaan yace "Lafiya kuwa?" Inna tace "Ina fa lafiya yaro an kacalcala kaji uku ba kudin da xa mu biya, nace ta mayar masu tsiyar su shine take kokarin tara min jama'ah wllh ko amsar ledan ma ni ban yi ba balle inji kamshin naman ciki, Toh a kan meye baxa su amsa ba? Dama haka ake yi?" Murmushi kawai mutumin yake yana kallon Imaan yace "Kazan guda nawa ne?" Da sauri Inna tace "Gudu uku ne wllh, daya nata daya nawa, daya na yan sa ido a gida..." Hannu ya sa a aljihu yana kallon Imaan, Mujaheed ya bude motar ya fita gun masu gashin kajin ya fiddo dubu biyar ya mika masu, daga Inna har mutumin da imaan bin sa da kallo suka yi, Inna tace "Kaga katon banxa ko? Ce mana yyi ba shi da kudi fa har sai da ya bari duniya ta gama sanin abinda muke ciki sannan ya fita wani zokai zokai da shi xai bada kudi, Toh Allah ya saka min kunyata ni da ya so yi gaban masu kaji da tona min asiri da yyi a gabanka" Dariya mutumin ya dinga yi yana kallon Inna da ta tsuke fuska tana kallon Mujaheed, imaan ta kalli mutumin gabanta ta mayar masa da kudin da ya mika mata tace "Mun gode" Yana murmushi yace "Don't worry...." Dawowa Mujaheed dake kallonsu yyi ya amshi kudin hannun imaan ya kamo hannun mutumin ya saka masa a ciki yace "Thanks for ur concern" daga haka ya bude mata front seat yana kallonta, ta sunkuyar da kanta ta shiga ya rufe motar, ya xaga ya shiga motar ya tada ya bar wajen. Inna tace "Ni dai duk wanda niyyarsa ya kunyata ni a duniya Allah ya min kantangar karfe da shi, kuma ya saka min" Shi dai Mujaheed bai tanka ta ba har suka isa gida. Shirye shiryen biki aka shiga yi a gidan ba kama kafar yaro barin bangaren Umma da kawayenta, ji take kamar an mata albishir da aljanna xata aurar da first and only son dinta xuwa ga 'yar masu kudi ba na wasa ba, shi ko gogan kamar ba shi xai yi aure ba babu Shirin da yake, idan ya fita aiki tun safe dama sai dare xai dawo don kawai bai son participating a shirin da ake a gidan, shi gaba daya bai fi sau uku suka hadu da Safeenar ba ma, kuma duk Umma ke tilasta sa sai yaje, ko da wasa bai taba dialing lambar Safeenah don kansa ba sai idan yayi missing call dinta, a rana kuwa tana kiransa fiye da sau goma, shi kansa mamakin irin son da take masa yake duk da yasan dole ta fahimci fa baya yinta amma duk class dinta bata nuna ta damu ba sai kara shige masa take. Tun ranan da Mujaheed yyi ma Imaan warning ko da wasa bata son Sadeeq ya xo kofar gidansu sai dai waya amma abinda ke bata mamaki yanda taga shi ma bai damu ya xo ba kamar da, da kusan kullum sai ya xo, sai dai suna kusan raba dare suna waya da shi cikin duvet yanda Ammi baxata ji ba, Duk Friday day kuma sai ya aiko wani worker din gidansu gun Inna ya kawo mata sako, Imaan dai ta tasan soon Mujaheed xai yi aurensa ya kara gaba sai taga ta yanda xai hanata tsayawa da Sadeeq kuma. Yau Friday da ya kama saura sati daya bikin Mujaheed da Safeenah Imaan ta fito daga dakinta ta shiga na Ammi, durkusawa tayi kusa da gado tana kallon Ammi tace "Ammi xan wuce yanxu" Ammi tace "Toh na dai gaya maki kar ki dade imaan" tace "Wallahi baxan dade ba Ammi" Ammi tace "Toh ki gaisheta Ina mata ya jiki" Imaan tace "Toh xata ji" mikewa tayi ta fita daga dakin ta shiga kitchen ta dauko wani leda mai dauke da can malt ta fito parlor ta dau jakarta sannan ta fita gidan, kamar mai tausayin kasa ta isa bakin titi bayan few minutes ta samu adaidaitan da xai kai ta GRA, tafiyar kusan minti ashirin suka yi, suka shigo gate din layin as usual ko ina tsit sai haushin karnuka, dai dai gate din kantamemen gidan Imaan ta sa mai adai daitan ya tsaya ta sauka ta basa kudin tana kallon masu gadi dake xaune bakin gate din gidan, gaishesu tayi daya daga cikinsu yace "Wa kike nema?" Tace "Mariya" Mai gadin yace "Toh ki kirata" shiru tayi tana kallonsa don kwanaki da dadewa da ta xo ae basu mata tambayar komai ba, ba musu ta fiddo wayarta a jaka ta shiga Kiran Mariya, Ba a dau lkci ba sai ga Mariya ta fito gidan, Rungume imaan tayi tace "Welcome frnd" tana kallon masu gadin tace "Kawata ce duk ranan da ta xo ku bar ta shigo babu interrogation" bata jira cewarsu ba ta ja hannun Imaan cike da farin cikin ganinta suka wuce ciki, Imaan tace "Dama kin ma ji sauki koh?" Mariya ta marairaice tace "Yau fa nayi getting self dina" Imaan na murmushi tace "Toh Allah ya kara lafiya" sai da ta fara kai Imaan dakin Mahaifiyar ta ta gaisheta sannan ta ja ta xuwa makeken bedroom dinta, imaan ta xauna tace "Siblings din ki fa?" Tana fiddo ruwa da lemo a fridge dinta tace "Sun fita da Yaya Annur shan ice-cream kinsan yau Friday" murmushi kawai Imaan tayi, Mariya ta ajiye mata drinks din tace "Me xa ki ci, akwai yam with sauce, cous cous with sauce, or kin fi son snacks?" Imaan ta girgixa kai tace "A'a na ci abinci a gida" Mariya ta harareta tace "A'a ni dai sai kin ci wllh" Imaan tayi dariya tace "Bayan nace maki na koshi, Ni la'asar kawai xan yi" Mariya ta nuna mata bathroom dinta tace "Kiyi alwala ga bathroom kafin ki fito xan kawo maki abincin" bata jira cewar Imaan ba ta fita da sauri, Murmushi imaan tayi ta mike ta cire Hijab din jikinta ta ajiye ta shiga bathroom din, tana gama alwala ta fito dai dai nan aka bude kofar dakin, still tayi tana kallonsa, kamar yanda shi ma ya tsaya yana kallonta, juya masa baya tayi da sauri tana xaro ido.... *Imaan isn't for free* it's 300 via Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah Then u show ur evidence of payment via my WhatsApp number 07087865788Sadeeq yayi murmushi a hankali yace "But you didn't tell me you where coming here da muka yi waya daxu" Ta dau hijab dinta ta saka still bata juyo ba tace "Ae ba wajen ka na xo ba" murmushi kawai yake yana kallonta, Mariya ta iso bakin kofar rike da tray din abinci tace "Ya Sadeeq Aunty na neman ka fa" ya kalleta yace "Har kin ji sauki kenan" dariya tayi tace "Ehh mana bayan alluran da ka sa aka min, Kuma ga kawata ta xo, Hope yau dai ka tuna ta" Ya langwabar da kai yace "Bayan ta ki juyowa ma in ga fuskarta balle in san wacece" Mariya ta wara ido ta kalli Imaan da ta ki juyowa da gaske, ta yi dariya ta karasa cikin dakin ta ajiye abincin hannunta ta isa kusa da Imaan ta juyota suna facing Sadeeq tace "Toh ka gane ta yanxu?" Shafa kai yayi yana cute smile dinsa yace "Anya.. wani anguwar take? Na taba ganinta ma kuwa?" Imaan bata san lkcn da tayi murmushi ba ta sunkuyar da kanta, Mariya ta bata fuska tana kallonsa don da gaske bata ji dadi ba, Sadeeq ya wara manyan idonsa yace "Toh Sannu da xuwa kawar Mariya, duk da dai ni ban gane ki ba" daga haka ya juya ya rufe masu kofar, duk yanda Mariya tayi forcing din Imaan ta ci abincin da ta kawo mata kin ci tayi wai ta koshi, ruwa kawai ta sha shi ma sip daya, Mariya da gaba daya bata ji dadin kin cin abincin da Imaan tayi ba tace "Dama ki dau drinks dinki ki koma da su bana so da gaske" dariya kawai Imaan tayi ta mike tace "Sai ki ba su Hafsat idan sun dawo, ni dai tashi ki rakani" Mariya tace "Bayan kin walakanta ni xa ki ce in raka ki" Imaan na murmushi ta nufi kofa tace "Toh ni fa na ci abinci a gida nace maki Mariya" Mariya ta mike ta bi bayanta suka fita dakin tace "Toh mu je ki yi ma Aunty sallama ya na iya da ke, nima dai ko ruwa kika ban idan naje gidan ku baxan sha ba" Imaan ta kalleta ta gefen ido tana murmushi suka shiga parlon mum dinta, Sadeeq na parlon tare da mum din nata a xaune, Imaan ta durkusa kusa da kujera tace "Aunty xan tafi" Mum din Mariya tace "Da wuri haka Imaan, toh Ina xuwa" tashi tayi ta tafi dakinta, Imaan ta sata kallon inda Sadeeq yake taga kallonta yake, ta dauke kai da sauri, Mariya tace "Ya Sadeeq yanxu fa su ya Annur xa su iya dawowa basu kawo min komai ba ko?" Yace "Toh ki kirasu mana" Tace "Toh don Allah kira min su ta wayarka, I can't imagine me not eating shawarma today" yace "Wayana na can gida" tashi tayi ta bi mum dinta daki don daukan wayarta ta kira step brother din nata, Sadeeq na kallon Imaan yace "Me yasa baku xo tare da kaka ba?" Ta dai yi murmushi bata ce komai ba, Aunty ta fito rike da leda ta ajiye kusa da Imaan tace "Ki gaida min mum din ki kinji Imaan" a hankali Sadeeq yace "Aunty ita ce fa warce nake yawan baki labari a kai...." Aunty ta kalli Imaan sannan ta kallesa da mamaki tace "Imaan din kuma?" Yana murmushi yace "Sure..." Sake baki tayi tana kallonsa, ya shafa kansa yace "Dama nace maki ba ma sai na kawo maki ita ba da kanta xata xo wataran ki ganta" Imaan taji kamar kasa ya bude ta shige don kunya, ta kasa dago kanta ta kalli Aunty, Aunty tace "Ikon Allah, wai da gaske kake don Allah Sadeeq" Yace "Gata ki tambayeta, but aunt this is our secret ko Mariya kar ki gaya ma plss Aunty, you know Mariya talks a lot...." Dariya kawai Aunty tayi ta xauna tace "Ikon Allah, Toh Allah ubangiji ya sanya alkhairi, yayi xabi na gari..." Yace "Ameen" Mikewa yayi yana kallon Imaan yace "Let me drop you" da sauri ta girgixa kai sai dai bata ce komai ba, Aunty tayi dariya tace "Aa ki je dai ya ajiye ki gida Imaan, ki gaida mutanen gidan kin ji, Allah maki albarka..." Sadeeq na murmushi ya nufi kofa ya fita, Aunty na kallon Imaan tace "Imaan idan ma kina da doubt a kan Abubakar a da, tohh stop that now kinji daughter, Sadeeq na son ki fiye da yanda kike tunani, I was so surprise da naji yace min ya sami yarinyar da yake so da aure yar Nigeria, coz ni nasan waye Sadeeq, I know him fiye da uwar da ta haifesa ma, kuma wllh duk jinsa nake ba wai na yarda ba, har gajiya nake da jin labarin ki a bakinsa, But plss kiyi kokarin kame kanki ki kare martabar ki na 'ya mace, am not saying this bcos Sadeeq is bad or anything of such, A'a Ina gaya maki haka ne a matsayina na uwa, ko Mariya iyakar shawarar da xan bata kenan...." Imaan dai ta kasa dago kanta, fitowar Mariya yasa Aunty tayi shiru, Aunty na kallonta tace "Ki rakata compound Sadeeq xai ajiyeta gida yanxu, he is waiting for her" Imaan ta mike tayi ma Aunty godiya cikin sanyin murya ta fita, Mariya ta dau ledan da Aunty ta ajiye mata tace "Mun gode Aunty" daga haka ta bi bayan Imaan da sauri, Mariya ta bata fuska ganin bata ga Sadeeq a bangarensu ba, tace "Kai ya Sadeeq maimakon ya dau motar dake nan yanxu sai mun bi sa har can" ita dai Imaan bata ce komai ba, haka suka dinga tafiya a lafcecen compound din xuwa bangarensu Sadeeq, Building din ya kusa biyun nasu Mariya, Kai kana gani kasan an rasa yanda xa ayi da Naira kuma, Motocin dake parking spaces din wajen sun yi goma ko wanne kuma ya wuce a kirasa mota sai dai Ride, ni kam nace don ma Inna bata xo taga gidan ba... Ai da gobe gobe xata sa Bukar da Ahmadu gaba ta tada bala'i a daura auren Imaan da Bulasawa... Lol, Sadeeq na xaune cikin daya daga motocin parking space din idonsa a kan Imaan dake tahowa tare da Mariya, irin kallon da yake mata yasa Mariya ta kalli Imaan sai dai bata ce komai ba, ana haka aka bude gate din gidan wani ride ya shigo compound din, Mariya tayi ma motar kallo daya ta dauke kai, Drivern yyi parking aka bude back seat, wata da baxata wuce shekaru hamsin ba ta sakko motar cikin shiga ta alfarma, tun daga kunnenta, wuyarta, finger, da wrist duk gold ne, tun da Imaan ta kalleta sau daya ta gane Mahaifiyar Sadeeq ce, Mariya tace "Sannu da dawowa Mami..." Sama sama matar ta amsa, Imaan ma ta gaisheta, ba tare da ta kalli Imaan ba ta amsa, tana kallon Sadeeq tace "Fita xaka yi yanxu Abba..." Ya fito daga motar yace "Welcome back Mami" tace "Yauwa..." Yana shafa kansa yace "Aunty tace in ajiye bakuwarta a gida..." Daga sama har kasa ta kallesa bata dai ce komai ba ta nufi entrance din babban gidan, ya bi ta da kallo, can yace "Mami xa a maki wani abun ne?" ba tare da ta juyo ba tace "Noo ka tafi inda aka aike ka, ka sameni parlona dai idan ka dawo, is Annur back?" yace "I don't think so" Front seat ya xaga ya bude ma Imaan yana kallonta, Mariya ta ajiye ledan hannunta a bayan motar ta xaga gun imaan tace "Plss kice ma Ammi ina gaisheta kin ji" Imaan ta shiga motar tana murmushi tace "Toh xan gaya mata" Sadeeq ya tada motar suka fita compound din Mariya na daga masu hannu, Sai da suka hau saman titi murya can kasa yace "Nayi missing din beautiful face din ki two days Imaan" Murmushi kawai tayi, yace "ke ko naga ma baki damu da rashin xuwa na ba koh? You won't even understand what I am going through now" Ta kallesa a hankali tace "I thought you are busy this days ne shi yasa" girgixa kai kawai yayi, bayan kusan minti biyar yace "My birthday is coming soon...." Ta kallesa tace "When" yace "7 days from today in sha Allah" shiru tayi don ranan daurin auren Mujaheed kenan, can tace "Toh Allah ya kai mu lafiya" yace "Anything for me?" Murmushi tayi tace "Me kake so?" Murya can kasa yace "Ke nake so Imaan" ta wara ido tace "Ni kuma" ya gyada kai yace "I don't know... i just have this urge of wanting to be with you, sai yanxu nake ganin nisan kwanakin da suka rage... I want you by my side as my wife" kasa kallonsa tayi ta kuma kasa cewa komai, ya kamo hannunta yace "Kin yi shiru" kwace hannunta tayi a hankali still ta ki cewa komai, parking taga yayi ta juya tana kallonsa, yayi kasa da murya yace "I am thinking of meeting grandmum, ko xata kara yi ma su Abba magana" Imaan ta kallesa da sauri tace "Maganan me?" Yana kallonta yace "Su yi hakuri su bani ke any time from now, wllh har professor xan iya barinki ki xama a gidana" Imaan ta girgixa kai kamar xata yi kuka tace "A'a ni dai, bayan ga abinda daddy na yace" Shiru yyi yana kallonta, cikin sanyin murya yace "Toh shikenan i will continue waiting and having patient in sha Allah" Driving ya ci gaba da yi, sai da suka kusa layinsu yace "My frnds are throwing a birthday party for me, kuma ke ce babban guess a wajen ranan" ta wani xaro ido tana kallonsa yace "Yea, don't turn down my offer baxan ji dadi ba....." Kasa cewa komai tayi yana shigowa layinsu gabanta yyi mugun faduwa, what if Mujaheed na waje yanxu haka, kafin ya isa kusa da gate dinsu da sauri tace "Kawai ma ka ajiye ni a nan ba sai ka karasa can ba" ya kalleta yace "Why?" Ta hadiye abu da kyar tace "Nothing" Bai ce komai ba ya kai ta har bakin gate din ta fara kalle kalle kamar munafuka ta bude motar ta fita yace "Wait Imaan" tsayawa tayi ya juya ya dauko ledan da Mariya ta ajiye mata, Mika mata yayi ta amsa tace "Nagode sai anjima" daga haka ta shige cikin gidan da sauri har hakan ya basa mamaki ya bi ta da kallo, tana shiga kuwa ta kulle gate din, sai da xuciyarta ya kusa shigewa cikinta ganin Mujaheed da Yusuf a compound din, Yusuf na xaune kan farin kujera Mujaheed kuma da alama gate xai fita amma sai kallonta yake, bata tsaya wani tunani ba ta fasa wani ihu ta sake ledan hannunta ta durkushe wajen tana yarfe hannu tana kiran Ammi, Mujaheed ya karasa inda take da sauri yana kallon kafarta yace "Me ya faru??" Ta kamo hannunsa tace "Wayyo Yaya kafana ban me ya same shi ba..." durkusawa yyi ya daga dogon hijab din jikinta yana kallon kafar, ta gefen ido ta dinga satan kallon kasan gate taga ko Sadeeq ya gama reverse. *Imaan isn't for free* it's 300 via Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah Then u show ur evidence of payment via my WhatsApp number 07087865788Imaan ta kwace kafarta a hannunsa bayan ta ga Sadeeq ya wuce tana turo baki a hankali tace "Ni ya ma daina, dama gurdewa kawai nayi" bata jira cewarsa ba ta mike da kyar, Yusuf dake tsaye shi ma ya iso wajen yyi murmushi yace "Dama ba wani ciwo, ke dai kika san abinda kike boyewa a waje" Mujaheed ya kalleta ya kalli gate da sauri, ledan da ta jefar ya dauka ya bude yana kallon abinda ke ciki, sai kuma ya nufi gate din.... Tana ganin haka ta dau ledarta da takalmanta ta wuce apartment dinsu da sauri tana waigan Mujaheed, Yusuf yyi murmushi ya koma ya xauna, Parlor ta tadda Ammi xaune, Ammi ta amsa sallamarta tace "Meye kuma kike sa min makulli a kofa" ta xaro ido tace "Ohh na manta, nayi xaton dare yyi..." Still dai bata bude kofar ba tana murmushi ta karasa cikin parlon ta xauna tace "Ammi Sannu da gida" Ammi tace "Yauwa, ya mai jikin?" Imaan tace "Da sauki, Mum dinta tace in gaishe ki, ta ma bani wannan" tana fadin haka ta ajiye ledan a kusa da Ammi, Ammi tace "Toh Allah ya amfana" mikewa Imaan tayi ta wuce daki har sannan xuciyarta bai daina bugawa ba, yanxu da Mujaheed ya ga Sadeeq ya xata yi yau. Tun bayan da ta idar da sllhn magrib Ammi ta ce ta dau abincin Inna ta kai mata gabanta ke faduwa, har claiming ciwon kafa tayi duk don Ammi ta kira Maimoon ta kai ma Inna abincin amma Ammi tace ita dai xata daure ta kai a hakan, tana goge guntun hawayenta ta dau abincin ta fita a sanyaye, ita kanta bata gane wani sabon tsoron Mujaheed da ya diran mata yanxu ba, a hankali ta bude kofar parlon Inna ganin takalmin da bata dai san ko na waye ba bakin kofar, ta ajiye abincin a nan bakin kofa Inna na tambayar wani munafukin ne amma tuni ta juya da sauri har tana tuntube ta koma part din su. Washegari Saturday karfe takwas saura Imaan ta fito bangarensu cikin shirin islamiyya, duk gaba daya a tsorace take har Ammi ta lura da hakan amma da ta tambayeta damuwarta sai cewa tayi ita bayanta ke mata ciwo, Ammi ta sa ta sha magani sannan ta fita, parking space ta dinga lekawa ko xata hango motar Mujaheed, ganin motar tasa yasa ta ki jiran su Maimoon ta nufi gate da sauri, ta gwammace ta tafi bakin titi ta samu adai daitan da xai kai ta islamiyyar. Suna jiran drivernsu bayan an tashi islamiyya Maimoon tace "Imaan wai me yasa kika ki jiran mu daxu?" Imaan ta tabe baki tace "Salon kawai ku 6ata ma mutum lkci mu yi ta yin latti ana xane mu, naga baku fito ba ni kuma bana son inyi latti shi sa nayi wucewata" Rahma tace "Har akwai wanda ya kai ki saka mutum yin latti? Kullum sai mun yi ta jiran ki bakin mota kafin ki fito, daga ace bayan ki ya rike sai ace kafar ki ya rike, to daga yau ma kar ki sake jiranmu kiyi wucewar ki" Imaan ta kalli Maimoon tace "Kin ga dai ba da wannan matar nake magana ba ko, ki gaya mata ba ruwanta da harkata tayi ta kanta ta kyaleni..." Rahma tayi dariya tace "Ehh gwara in kyaleki kiji da ciwace ciwacen ki kam....." Maimoon ta kalli Rahma tace "Haba meye haka Rahma?" Rahma ta watsa mata wani kallo tace "Sai dai ki tambayeta meye haka, ko ni sa'arta ce aka gaya mata??" Tsaki tayi ta wuce gun motar gidan su da yyi parking dai dai lkcn, Ummi ta ja tsaki tace "Mutum sai neman fitina kawai, ana taba ta kuma lalura ya tashi a shiga uku, to dama wa xai taba sauran ciwo idan ba tsautsayi ba ma" tana fadin haka ta wuce ta shiga mota ita ma, Maimoon ta kalli Imaan dake kallonsu tace "Ki rabu da su kiyi hakuri" Imaan bata ce komai ba ta bude front seat ta shiga Maimoon ma ta shiga back seat... Suna isa gida driver yyi parking Imaan ta bude motar ta fita bata xame ko Ina ba sai part din Inna, Inna na xaune parlon tana hada kwadon rama Imaan ta shigo ta xube nan kan kujera ta fashe da matsanancin kuka, Inna ta tura roban gabanta tace "Auzubillahi, me ya sami Aishar?" Cikin kuka Imaan tace "Ko ba su Rahma da Ummi bane daga Ina magana da Maimoon suka fara xagina har da ce min sauran ciwo...." Mikewa Inna tayi ta rufe roban kwadonta ta dau gyalenta ta nufi kofa ta fice, Imaan ta dinga kuka har da shessheka, can dai tayi shiru ta goge idonta ta shiga kitchen ta dauko wani plate ta debi kwadon da Inna ke hadawa ta fice a parlon. Babu abinda Inna ta mance bata xaxxaga ma Umma dake dakinta a xaune tare da su Ummi dake mata tsarin abinda ya faru tsakaninsu da Imaan, Inna na huci tace "Kuma in sha Allahu sai kinga sauran ciwo a jikokin da xa a haifa maki..." Da sauri kuma tace "Astagafirullah, jikokin ki ai na Ahmadu ne, to in sha Allahu sai kinga sauran ciwo a dangin ku.... Kuma a kawo maki riko kiyi ta fama, duk wanda ya sake sa min jikata a bakin duniya Allah ya isa ni dai, Allah ya isa, kuma bari Ahmadun ya dawo...." Tana fadin haka ta fice. Imaan na shiga apartment din su ta tadda Ammi na ta girke girke, gaisheta kawai tayi ta wuce daki, tayi wanka tayi sllh sannan ta shirya ta fito parlor, kitchen ta shiga gun Ammi dake hada drink din Zobo tace "Ammi jirgi daddy xai biyo ko train?" Ammi tace "Ce maki yyi xai dawo yau?" Imaan ta xaro ido tace "Naga kina girki ne ai" Ammi tace "A'a mamar ku ce dai ke hanya...." Imaan tace "Mama Hadiza?" Ammi tace "Ehh sun ma kusa landing Ina ga" Imaan ta wara ido tace "Shine Inna bata gaya min ba?" Ammi tace "Ita ma bata sani ba shi yasa ban gaya maki tun jiya ba kar ki je ki gaya mata don ba control gare ki ba" Murna Imaan ta dinga yi tace "Da su Maryam xa ta xo in gansu plss?" Ammi tace "Da Maryam kadai suka taho" Imaan tace "Toh wa xai je daukota a airport nima xanje plsss" Ammi tace "Mujaheed Daddy yace yaje ya daukota" shiru Imaan tayi bata ce komai ba, can ta dau plate ta bude abinci xata diba. Hudu na yi Mujaheed ya tafi airport dauko small mum din tasa da autar ta, tun da suka kamo hanyar gida Maryam ke tambayar sa Imaan da turancinta dake kala da na turawa, yyi murmushi yace "Tana nan, tsayin ku daya sai dai ita bata jin magana..." Maryam ta kyalkyale da dariya tace "Ni duk na kagu in ganta wllh, muna fa vid call da ita once in a while" Mujaheed yace "Ae xa mu je ki ganta" Mama Hadiza tace "Amma dai yanxu ta ji sauki sosai koh?" Yace "Ehh mama da sauki sosai" Hadiza tace "Toh Alhmdllh haka Yaya Sadeeq din yace min, Toh in ji dai xa a kawo min amaryar mu gaisa kafin biki..." murmushi kawai yyi bai ce komai ba, tace "Au baxa ka kawota ba kenan" yar dariya yyi yace "Toh xa a kawota in sha Allah mama" Mama Hadiza tace "Toh da dai ya fi, kuna ta dai hakuri da tsufan Inna koh?" Mujaheed yace "Mu wllh da ma ki tarkatata ku koma tare mama" dariya Mama Hadiza tayi tace "Baka da kirki Mujaheed, ita uwar tawa kake cewa in tarkata?" Yace "Wllh mama duk ta addabi kowa a gidan..." Mama Hadiza tayi murmushi tace "In sha Allahu nan da wata hudu ma xa mu dawo Nigeria gaba daya sai in dauke uwata ta dawo wajena sai in ga ta inda xa ku dinga gajiya da ita" Mujaheed yyi dariya yace "Wllh baxata yarda ba, xata gwammace tayi ta xama tana dagawa Ahmadu da Bukar hankali" Mama Hadiza tayi dariya tace "Baka da mutunci wllh Mujaheed" parking Mujaheed yyi a parking space din su bayan sun isa gidan, Mama Hadiza tace "Allah sarki, rabona da gidan nan shekara uku kenan, anjima idan na huta da Magrib sai ka kai ni gidan Seeyama" yace "Toh Mama Allah ya kai mu" part din Abba Mama Hadiza ta fara shiga tare da Maryam don gaisawa da Aunty da Umma... Bata wani dau lkci a part din ba ta fito tare da Aunty, Umma dama tun bayan da suka gaisa ta shige daki ta kulle, Mama Hadiza na kallon Aunty tace "Rukayya dai na nan da rashin kirkinta har yanxu koh?" Dariya kawai Aunty tayi, Mama Hadiza tace "Toh yayi kyau ta ci gaba, har ni xata walakanta ta shige daki sbda bata da mutunci" ita dai Aunty bata ce komai, suka shiga part din su Imaan, Imaan ta fito daki jin muryar Maryam ta rungume ta cike da murnan ganinta, Ammi na kallon mama Hadiza bayan sun gaisa tace "Toh Ina jakar? Ko ba nan dama xa ku sauka ba" Mama Hadiza tace "Yana cikin mota Mujaheed bai fiddo ba" Ammi ta kai ta har bedroom dinta don ta kintsa, Aunty dai tayi masu sallama ta koma. Maryam na idar da sllh bayan ta ci abinci tayi wanka dakin Imaan, suka dinga hira... Ganin Magrib ya kusa Imaan tace "Plss mu je ki ba Inna surprise kawai ta gan ki" Maryam tace "Hope ta daina xagin mutane dai yanxu" Imaan tayi dariya sosai tace "Sai dai bata ga abinda xata xaga ba, ke dai mu je" A tare suka fito dakin suka wuce part din Inna ba tare da sun sanar da su Ammi dake bedroom ba, Inna na bakin tap suka iso bangaren nata, ta daga kai tana kallonsu, Imaan dai sai murmushi take, Inna tace "Waya wannan kuma kamar Zabiya?" Imaan ta fara dariya tace "Baki ganeta ba Inna?" Inna ta ci gaba da wanke wajen tace "Ka dai ji wata magana wai ban ganeta ba, yanxu ko uwata ce ta fito daga kabari idan ban ganeta baxan ce mata ban gane ta ba, tun daxu nake durkushe a nan nake aiki babu mai taimakona, baki ji bayana ba kamar ya balle in huta...." Maryam ta hade rai ta shige parlonta, Imaan tace "Maryam ce fa Inna" Inna tace "Waye kuma Maryam" Dariya kawai Imaan take tana kallon Inna, Inna tace "ita ce ta xama kamar zal6e?" Imaan ta xauna a balcony din tana dariya, Inna ta tabe baki tace "Ku dai baku son gaskiya a gidan nan, yanxu da ba don wannan yar albarkan Maimoon ta gaya min a boye ba daxu da baxan ma san Hadiza xata xo gidan nan ba, Toh kuma kya taho min da yarinya tsigi tsigi kice Maryam, Yar da aka haifa hannuna ce aka ce maki baxan gane ba, ni fa na mata wankan farko kuma a gabana aka yayeta..." Inna ta tabe baki tace "Ni dai ba ruwana" Fitowa Maryam tayi daga parlon ta yi wucewarta, Inna ta bi ta da kallo ta kyabe baki tace "Ubansu dai ya cuce su ya hallaka su, ya kwashe su ya tafi kasar tsinannu yayi kaka gida, toh tana ma jin hausar kuwa" Imaan dai ta kasa cewa komai sai dariya take, Inna ta gama dauraye bakin tap din ta mike ta shige cikin parlonta tana cewa "Bukar dai ya haifi jaraba, ba don naka naka bane ai ni bana bari a cuci Bulasawa a lika masa ke ba, to banda haka ni sa'ar uwarki ce xaki xauna bakin kofa kina babbaka min dariya kamar mahaukaciya?? ita ma Hadizar dama kada ta kuskura ta xo min nan xan koreta tunda bata maida ni bakin komai ba, banda haka ta kamo hanya rai kwakwai mutu kwakwai baxata gaya min ba in mata addu'a, wannan ba shawarar kowa bace illa wannan mutumi Bukar don shi ne me irin wannan tunanin na marasu nutsuwa, Amadu baya haka" mikewa Imaan tayi ta bar wajen ta koma part din su... Bayan magrib tare Abba suka tafi gun Inna da Maryam, Inna na xaune parlon tare da Mama Hadiza da Mujaheed, Inna na ganin Maryam ta washe baki tace "Yanxu nake rokon Mujaheed ya tashi ya nemo min ke don tun saukan ku bamu hadu ba kin xo daxu ina gurje bakin pampo ke kuma baki jira in gama ba kika yi wucewar ki" Maryam ta xauna ta gaisheta babu walwala, Inna ta amsa da fara'a tace "Kun sha hanya, sai kawai naga kin kusa kamo imaan a tsayi..." Maryam dai bata tanka ta ba, Mama Hadiza sai murmushi take, Abba ya gaida Inna ta amsa tace "Ae gwara da ba a gaya min suna hanya ba Ahmadu da baccin kirki ma ni baxan yi ba, amma da na gansu kamar daga sama ai yafi ko" Abba na murmushi yace "Gaskiya ne" Mikewa Mujaheed yyi ya fita parlon Maryam ta bi bayansa, a jere suke tafiya tace "Ya M.A kaga abinda Inna ta min daxu kamar bata taba ganina ba" Dariya Mujaheed yyi yace "Xata maki fiye da haka ma, so take it off ur mind plss haka nan take, ya karatu?" tace "Alhmdllh...." Ya kalleta yace "Hope baki kula samari sai kin gama karatun" tayi dariya tace "Kai ya M.A, bayan ga Imaan ma tana da saurayi, ta ma ce min xai yi birthday soon and his frnds will be celebrating it for him, wai in bata shawarar abinda xata basa" Tsayawa Mujaheed yyi yana kallonta, can yace "When tace maki birthday din?" Ta wara ido tace "I didn't ask her, mun ma gaisa da shi a waya yace xai xo gobe ya gaisheni, his voice is cute..." Tana murmushi ta kare maganar, Shiru yyi bai ce komai ba ya ci gaba da tafiya a hankali tana biye da shi, Xaro ido tayi tace "Wait... Am I even suppose to tell you this??" Yar dariya yyi yace "Me yasa kika ce haka?" Tace "Naga irin kamar you are surprise.... Kila ma baka san tana da saurayin ba ni ce na maka revealing koh?" yace "Yes.. boye mana take, Amma kar fa ki ce mata kin gaya min she won't be happy" Maryam ta marairaice tace "Toh nima kar ka mata magana about it she won't be happy with me...." Yace "Sure I won't" suna isa part din su Imaan tace "Am spending the night here, ka ce ma su Maimoon, Ummi da Rahma su xo muyi hira plss" yace "Ohk xan gaya masu" daga haka ya wuce, tafiya yake amma gaba daya abinda Maryam ta gaya masa ne ke yawo a ransa... Wani murmushi yyi ya shiga sashin su.Washegari da safe Imaan na kumbure kumbure ta gama shirin islamiyya bayan Ammi tace baxata xauna mata a gida ba, Maryam ta sami Ammi a kitchen a hankali tace "Ammi don Allah ki barta kar ta je yau, I don't have anybody to gist with idan ta tafi fa" Ammi tace "Ga kakarki can ki je ku yi hiran mana" da sauri Maryam tace "A'a ni bana son hirarta kawai tayi ta xagin mutane, nima ta fara xagina" Ammi tayi murmushi tace "She is ur grandma dai" Maryam tace "Sure, pls Ammi kin yarda kar taje?" Ammi tace "Karfe sha biyu xa su tashi ai, kuma sauka xa su yi soon Maryam, imaan ko shakkar fashi bata yi shi sa nayi forcing dinta ta wuce" Maryam tace "Ohk then, Allah ya kai mu 12 din" daga haka ta fita kitchen din, Imaan ta fito daki bayan ta dauko jakarta ta nufi kitchen ta tsaya bakin kofa kamar xata yi kuka tace "Ammi na tafi" Ammi tace "Breakfast din fa?" Ta girgixa kai tace "Ni sai na dawo" Ammi tace "Oho cikin ki" Juyawa imaan tayi ta fita, Maryam ta rakata xuwa parking space, dai dai fitowar Mujaheed da makullin mota a hannunsa, Maryam tayi masa murmushi tace "Good morning ya M.A" ba tare da ya kalleta ba yace "Morning Maryam kin tashi lafiya?" Tace "Sure.. Alhmdllh" Imaan dai tuni ta dauke kai, Maryam tace "Aiki xaka fita ya M.A" yace "Noo, sai da yamma nake fita aiki during weekends" Tace "That's nyc... Do you need my company?" Ya kalleta kamar baxai ce komai ba sai kuma yace "Sure... if that will suit you" ta kalli Imaan tace "Alryt sweetheart xan raka Ya M.A, ayi karatu da kyau a islamiyya" imaan ta kalleta tace "Ohk bye" tana fadin haka ta saci kallon Mujaheed taga kallonta yake, da sauri ta dauke kai, Ya bude motarsa ya shiga ya tada, Maryam ta xaga ta shiga gaba. Ko da Imaan ta dawo daga Islamiyya karfe sha biyu Maryam bata dawo ba, Imaan na kallon Ammi tace "Ammi wai tun da safe har yanxu Maryam bata dawo ba?" Ammi tace "Ehh wai sun fita tare da Mujaheed koh?" Imaan ta tabe baki ta mike ta wuce dakinta. Bayan azahar tana gama cin lunch ta tafi bangaren Inna, Inna na xaune parlor tare da Mama Hadiza, Imaan ta gaida small mum din nata sannan ta gaida Inna da ta tsuke fuska, Inna ta amsa tace "Ke kiji Hadiza da wani mummunan xance Imaan, wai duk abinda xa ayi na bikin Mujaheed mai kyau ko mara kyau in saka ido kar in yi magana, Saboda ita bata da tsoron Allah, bata son gaskiya xuciyarta ta kekashe, to me mutum xai min wanda Allah bai min ba" Mama Hadiza tace "Ni dai ki fahimce ni Inna, idan ba mu fada maki gaskiya ba kina da mai gaya maki ne, ba girman ki bane komai kika gani ki tanka a tafi da ke a baki, Haba inna" Inna tayi mitsi mitsi da ido tace "An dade ba a tafi da ni bakin ba, ni da bikin jikana ki dinga gaya min maganan banxa, ke kinsan wahalan da nayi da Mujaheed kuwa, wllh wllh ko Rukayya bata da iko da shi a yanxu, mutumin da yasa na dinga fada da jama'ah a anguwa yau ya kwale d'an wancan gobe ya danne d'an wancan, da ma Allah ya rufa min asiri bai sa an min duka a anguwar ba har Allah ya raba ni da anguwar? ke kinsan sau nawa na shirya na tafi makarantar su Mujaheed fada da malamai kuwa... Kishiyoyina kuwa duk min dambatu da su a kan Mujaheed, Sannan ace wai in xama kurma a bikinsa kamar uwata tace min je ki kya gani? To wllh karya ake...." Mama Hadiza tace "Ba ace ki xama kurma ba amma ba komai xa ki tanka ba, ba komai xaki shishshige ma ba, Allah na tuba Rukayyar da ma in don ta nata ne bata son a shiga lamarin bikin, ji fa tasan don bikin takanas na xo kasar nan amma tun sannu da xuwan da ta min jiya a bangarensu ban sake ganinta ba, ace kuma tayi farin ciki da xuwana...." Inna ta kunduma ma Umma xagi tace "Ai ba ita ke aurar da d'a ba nice nan mai aurar da Mujaheed kar ki ji komai, mu xuba kuma a gani, Allah dai ya kai mu ranan da rai da lafiya, sai dai mu kwashi yan kallo da ita a bikin nan idan kuma bata yi hankali ba dama baxata kwana gidan nan ba ranan bikin" Mama Hadiza ta tabe baki bata dai ce komai ba, Inna tace "Haka kawai, inyi wahala da shi a dinga gaya min maganan banxa" Imaan dai murmushi kawai take tana danna wayar hannunta, sallama aka yi bakin kofar parlon, Imaan ta juya da sauri jin muryan Sadeeq, Inna ta mike daga xaunen da take da sauri tana washe baki tace "A'ahhh sannu da xuwa Bukar, kai ne da ranan nan... Bisimillah shigo abun ka... Ba kowa daga ni sai Hadiza da Imaan" da gudu imaan ta shige dakin Inna, Sadeeq ya shigo parlon kansa a kasa, Inna na washe hakora ta kalli Mama Hadiza dake xaune kan kujera tace "Ke tashi ki basa waje ya xauna mana, sirkin ku ne" Sadeeq ya bude ido yace "A'a kaka ga waje ai" Bai jira cewarta ba ya xauna saman carpet dake shimfide, Inna ta nufi fridge ta bude ta kwaso ruwa uku da malt uku ta taho, Mama Hadiza dai sai bin ta take da kallo cike da takaici, Sadeeq na kallonta a hankali yace "Ina yini?" Mama Hadiza tace "Lafiya lau, Sannu da xuwa" Inna tace "Saurayin Imaan ne, jira kawai yake ta kare sakandari ayi magana, d'an gidan Ahmad Bulasawa ne mai gidajen man fetur a arewa, sunan yayanki garesa.... Baki ga kirkinsa ba, ni dai tunda nake ban taba cin karo da mutum mai kirki da mutunta babba irinsa ba" Mama Hadiza dai ta kasa cewa komai, Sadeeq dai ya sunkuyar da kansa sai murmushi yake, Inna ta kwalo ma Imaan kira tace "Ji walakanci, to meye na gudu daga jin sallaman bawan Allah, baxa ki fito ku gaisa ba, ba don ke ba a ina xa mu sansa" Imaan da ta xauna saman gadonta ta turo baki ta ki cewa komai, Sadeeq na shafa kansa yace "Dama baki na xo gaidawa kaka" Inna tace "Ahh toh madallah, Ka ganta nan xaune...." Ta fadi haka tana nuna masa Mama Hadiza tace "Uban Imaan ne ya sha nono ya bar mata, ita ce autata, yaranta hudu a duniya Allah yayi ma daya rasuwa, dayar tayi aure tana can gidan mijinta a kasashen turawa, sai kaninta da ke karatu sannan wannan yarinya Maryam da suka xo tare, sa'ar Imaan ce yarinyar kawai dai Imaan ta fita tsayi, ita kuma Maryam din ta fi Imaan xama mace" Tagumi Mama Hadiza tayi tana kallon uwartata, Sadeeq kam murmushi kawai yake kansa a kasa, Inna tace "Toh duk ba wannan ba, kana da labarin bikin Mujaheed wannan Juma'ah me xuwa ne kuwa Bukar?" Sadeeq ya kalleta yace "Ai kam bata gaya min ba kaka..." Inna ta saki salati ta rike ha6a tace "Kaga fitina koh? Duk da dai ko ta gaya maka ko bata gaya maka xa ayi bikin baxa a fasa komai ba amma ai da ta gaya maka, Toh ni dai na gaya maka yanxu, bikin ranan Juma'ahn nan ne" Sadeeq yace "Toh Allah ya kai mu lafiya kaka" Inna tace "Ameen dai, ai har ya kai ni gidan da xa su xauna da amaryar tasa ni da imaan mun gani, baka ga gidan ba d'an madaidaici dai dai kafinsa dai, toh ba dai laifi... ni dai nace Allah ya sanya albarka ai dai ya fi babu wai d'an agwai da bak'in da" Sadeeq ya kasa daina murmushi nan ko dariya ne kawai ke cin sa, Takaici yasa Mama Hadiza ta mike tana kallonsa tace "Toh Sadeeq nagode da gaisuwa Allah yayi albarka bari in shiga can cikin gida" Yace "Toh Ameen mama, nagode" fita tayi daga parlon, Inna tace "Toh ki ce ma Aisha don Allah tayi miyar shuwaka yau, naji raina na so" Mama Hadiza dai bata ce komai ba, Inna tace "Don Allah Imaan ki rufa min asiri ku fito ku gaisa, wannan ai kauyanci ne daga ganin saurayi ki shige daki, ni ko lokacinmu ba a haka" Sadeeq yace "Ki kyaleta kaka" Inna tace "In kyaleta d'an nan?" bata jira cewarsa ba ta mike xata shiga dakin, Imaan na ganin haka ta maxa ta sa hijab dinta ta fito, Inna tace "Ki daina haka don Allah sai ayi tunanin goyon kauye ce ke, nan ko a Habuja aka haife ki" Dariya Sadeeq ya fara yi imaan ta daure fuska ta xauna saman kujera a hankali tace "Ina yini?" Yace "Lafiya lau, ya gida?" Inna ta xauna tana murmushi tace "Gida Alhmdllh" kallonta Imaan tayi da sauri ta wani daure fuska, can ta kallesa tace "Let me see you off, since you've accomplished ur mission here today" Yana murmushi yace "I see why you don't want the 3 of us together..." Inna dai sai washe baki take tana kallonsu tace "Ae ita ma babban makaranta tayi, babu irin turancin da bata iya ba wllh" Mikewa Imaan tayi tana kallon Sadeeq tace "Let go" Mikewa yayi trying hard not to laugh yace "Toh kaka na gaishe da Mama da ke, ni xan koma" Inna tace "Ai mun gode da gaisuwa Bukar Allah maka albarka...." Dubu goma ya ajiye mata tayi tagumi tace "Ni dai na shiga uku Bukar baka gajiya??" kofa ya nufa yace "Ai ba yawa kaka, ayi hakuri" daga haka ya fita don tuni Imaan ta fice daga parlon, sai da suka bar part din Inna Sadeeq ya tsaya ya dinga dariyar da bai samu damar yi a parlor ba non stop, Imaan ta dinga kallonsa kamar xata yi kuka, ganin yanda yake dariya seriously ta jingina da flower tana ci gaba da kallonsa don bata taba ganin dariyarsa haka ba sai this very moment, he looks more cute laughing, bata san lkcn da tayi murmushi ba her eyes still on him, don kansa ya gaji ya dakatar da dariyar haka, a hankali tace "You look cute while laughing" da sauri ta rufe fuskarta bayan ta fadi haka, ya kafeta da manyan idanuwansa, kamar ta sani kuwa ta juya masa baya tana xaro ido, and he felt like hugging her tightly to himself, ya dai yi murmushi ya sauke kansa kasa praying in his mind Allah yasa xuwa wajensu Abba da xai yi tare da uncles dinsa in few days time won't be a futile effort... Takun da suka ji a bayansu yasa duk suka juya a tare, Mujaheed ne ke tahowa tare da Maryam, Sosai gaban Imaan ya fadi tayi still inda take, tunda ya kallesu sau daya ya dauke kai, Murya can kasa Sadeeq yace "Is she the Maryam?" Imaan ta gyada kai a hankali tace "Sure" Suna isowa inda suke Sadeeq ya mika ma Mujaheed hannu, Mujaheed na kallonsa ya mika masa nasa, Sadeeq yace "Ya aiki?" Mujaheed yace "Alhmdllh" daga haka ya wuce, Maryam ta gaida Sadeeq, Yana murmushi yace "It's nice meeting you Maryam, hope babu gajiyan hanya yanxu" Tace "Ba gajiya kam, kun fa dace da sis dita, Allah ya bar ku tare" ya wara ido yace "Ameen, I love those last words of urs... Kuma dole sai na biya words din, you say what ever you want ko menene idan kuma kin bar min xabi shikenan" ita dai Maryam dariya kawai take tace "Toh nagode Sadeeq" daga haka ta bi bayan Mujaheed da sauri, tana iskesa murya can kasa tace "Wllh he is just too cute Ya M.A, Imaan is very lucky..." Mujaheed bai tanka ta ba ya bude kofar parlon Inna ya shiga ta bi bayansa, tana cewa "Nama san me xan ce Imaan ta basa for his birthday...." Kallonta yayi yace "Me xaki ce mata.." ta kashe masa ido tace "That's our secret big Bro" Xaunawa yyi saman kujera yana kallon Inna, Inna tace "Yanxu wannan yaron dake neman Imaan ya fita, baka ga yanda ya dinga fada imaan bata gaya masa bikin ka ranan Juma'ah bane, gaba daya bai ji dadi ba, Allah kadai yasan me Bulasawan da kansa xai baka, mutum miloniya meye kuma baxai bada ba" a fusace Mujaheed yace "Sai dai ya baki ke da kike bukata, amma ni bana bukata, kuma don Allah kiyi hakuri ki daina maganata a gaban mutane bana so, ni abinda nake da shi ya isheni xaman duniya ba sai na hangi na wani ba" Yana fadin haka ya fice daga parlon, Inna ta tabe baki tace "Uwarka Rukayya ka gaggatsa ma magana ka fita ba ni ba wllh, ba abinda ya hada ni da kai dama, kawai Ahmadu ne ya haifeka ni kuma na haifesa, Ni ban yi mamaki ba tunda goyon Rukayya ce kai din ai, xaka yi fiye da haka" Maryam na dariya ta mike ta fita a parlon ita ma, da daddare Imaan na fitowa daga wanka daure da towel tace "Wai ina kuka je daxu da yaya tun safe" Maryam dake operating laptop tace "Wato kina wanka hankalin ki na wajen ki fito kiyi tambaya" Dariya Imaan tayi tace "Eh mana" Maryam ta ajiye laptop din a gefe tace "Ae babu inda ba mu je ba..." Imaan tace "Kamar Ina da Ina?" Maryam tace "Ya fa ce kada in gaya ma kowa har ke" Imaan ta xauna kusa da ita tace "Don Allah ki gaya min, ai ba gaya masa xan yi ba" Maryam tayi dariya tace "Anya xan iya gaya maki kuwa, ce min fa yayi amana, kuma sbda ke muka je wajen...." Imaan kamar xata yi kuka tace "Don Allah ki gaya min, wllh baxai sani ba, abinda ma ba shiri muke da shi ba yanxu" *Imaan isn't for free* it's 300 via Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah Then u show ur evidence of payment via my WhatsApp number 07087865788Maryam tayi dariya tace "Kai Imaan haka kike da son jin abinda bai shafe ki ba?" Imaan ta marairaice mata tace "Ni dai ki gaya min" Maryam na murmushi tace "Ke ba ko ina mu ka je ba, kawai dai ya kai amaryar tasa plazan da xa ayi mata dinkunan bikin ne ya bada kudi, sai kuma gold na rings guda uku da ya siya mata for the wedding, sannan muka koma gida muka ajiye ta, after that muka je kasuwa siyo drinks da Ummansa tace ya siyo, sai flasks da bedsheets da xata yi souvenir ma kawayenta....." Imaan ta ja tsaki tace "Toh meye na cewa kar ki gaya min, ko ni ina ruwana?" Maryam tace "Ke wasa nake kawai Inna yace kar in gaya ma amma ba ke ba" Imaan ta mike tana goge jikinta tace "Toh shine xa ki ce saboda ni ku ka je inda ku ka je?" Maryam tace "I am just pulling ur legs, kin taba ganin amaryar tasa kuwa?" Imaan tace "Ehh na taba ganinta a gidansu" Maryam tace "She is beautiful but her fairness isn't natural" Imaan tayi dariya tace "Artificial ne kenan" Maryam tace "Probably... And she isn't friendly, she didn't even acknowledge my present sosai, kamar bata son mutane, sai kin ga ma yanda ta amsa min gaisuwan da na mata, she just shunned me..." Imaan tace "Tohh ba sai ki fasa bin su ki dawo gida ba, Toh me yayan yace?" Maryam tace "He couldn't say anything to her, amma shi ma naga bai ji dadi ba, coz he even introduced me to her again, amma ta ki cewa komai" Rai bace imaan tace "Toh wai me yasa baki dawo gida ba??" Maryam tace "Ae ban san hanya ba, beside I am not with money, ga shi in gaya maki sai wani shagwaba take masa a mota, shi ko a cikin magana goma bai fi ya amsa mata uku ba" Imaan tayi dariya tace "That's their problem" Maryam tace "Yea least I forget, na yi maki deciding abinda xa ki siya ma Bf din ki for his birthday" Imaan na shafa lotion dinta tana kallonta ta madubi tace "And what's that?" Maryam tayi murmushi tace "But wait... did he invite u for the birthday party?" Imaan ta gyada mata kai, Maryam tace "Kuma xa ki je?" Langwabar da kai Imaan tayi a hankali tace "Toh I haven't decided yet, ban sani ba tukun" Maryam tace "Toh after ur decision xa a bar ki kije a gida kuwa?" Imaan ta xaro ido tace "Dama wa xan gaya ma?? Tab... Am telling nobody" Da sauri ta dawo kusa da Maryam ta xauna tace "Plss Maryam wannan ya xama sirri tsakanina da ke, Kinga even Maimoon da ta ke kawata ma ban gaya ma ba, don Allah kar by mistake ki ce ma Ya Mujaheed anything about the birthday" Shiru Maryam tayi tana kallonta, hankali tashe Imaan tace "Ko dai har kin gaya masa?" Maryam tayi yake tace "Haba dai why will I, of course ban gaya masa komai ba" Imaan ta sauke wani ajiyar xuciya tace "Better" Maryam tace "May be... A day to the birthday sai mu fita babban shopping mall in nuna maka abinda ya kamata ki siya masa" Imaan tayi shiru tana tunani, can tace "Toh Allah ya kai mu" kayan baccinta ta saka ta hau saman gadon ta dawo kusa da Maryam tana kallon abinda take yi a laptop dinta. Slowly ranakun suka dinga tafiya har ya rage saura kwana biyu bikin Mujaheed da Safeenah, gida ya cika da Yan uwa da abokan arxiki, matan kawu Bala, Hansai da yaranta kai duk yan uwa dai an cika gidan barin part din su Umma, duk inda kaga Imaan toh xaka ga Maryam a gidan kamar da can sun saba da juna sosai, seriously Mujaheed ya sa ma Imaan ido a gidan, ita kuwa ko sanin yana yi bata yi ba. Da yamma Imaan na parlon Inna tare da Maryam sun kawo mata abinci, sai bin Inna dake ta neman makullin bandakinta suke da kallo, duk ta hada xufa ta wani tsuke fuska, komai sai da ta daga a parlon amma babu makulli babu labarin sa, Mama Hadiza ta fito daga daki da alamar ita ma neman makullin take tace "Toh wai ina kika ajiye makullin Inna?" Inna tace "Ke ki rabu da ni don Allah, nasan inda na ajiye xan ta neme neme, da ba don rubabbun dake shigo min nan ba har xan wani kulle bandaki kamar warce ta ajiye gwalagwalai a ciki har shegen makullin ya bata?? Ni dai ba ruwana a ma daina xuwa min nan gaba daya, tunda ba ni ke aurar da mutumi ba" Dariya Maryam ta dinga yi Inna ta daga kai daga duken da take tana kallonta, Sallama aka yi bakin kofa Inna ta mike tsaye ta amsa sallaman, Ta rasulu ta shigo tana kyabe fuska, Rahma ta ajiye mata karamin jakarta ta juya ta fita, Inna na washe baki tace "Sannu da xuwa Ta Rasulu kinga na rasa inda na jefa makullin bandaki, gudun kar a shigar min bandaki na kulle na saka makullin a bakin zani to yanxu gashi ko sama ko kasa" Ta rasulu tace "Toh ai gwara da aka nema aka rasa gaba daya, kinga bayan bikin sai a balle kofar kawai, don wani na iya xuwa ya maki dadin baki ki kunce makullin ki basa, mutane dai basu gaji mutunci ba, kinga yanda aka 6ata tsakar gidan da shinkafa ga yara jage jage kamar daga kauye, ni dai ba kowa ma ya kamata a dinga bari yana shigowa ba ma wllh, sai kace ba bikin yan gayu ba" Inna tayi tagumi tace "Naga abinda ya isheni, kin ji wata fitina koh, Kai mutane dai jarababbu ne, kice tsakar gida na nan duk wari?" Ta rasulu ta tabe baki ta wuce cikin dakin tace "Ae kuma sai ki yi, abinda tsoron Allah yayi karanci a xukatan mutane yanxu" Inna tace "Toh ni kuwa xan je in basu hakuri su rufa mana asiri kada gidan 'ya yana ya lalace mu shiga uku, sannan biki dai ba ace a xo da yara ba" Mama Hadiza ta leka dakin ta gaida ta rasulu sama sama ta fita parlon gaba daya, Imaan ta tabe baki xata tashi Inna tace "Toh ke kin gaida ta rasulun ma kuwa" daga cikin daki ta rasulu tace "Ina fa ta gaida ni tana kallona ina kallonta, yaran yanxu kam sai ka kyalesu, mu dai muna masu fatan alkhairi Allah kuma ya basu miji na gari, har wannan figaggiyar ta kusa da ita ma ni bata gaisheni ba ai" Imaan ta gaida ta daga inda take tana turo baki ta mike ta fice a parlon, Maryam ta mike ita ma ta gaidata ta fice Inna na cewa "Iyayenku ku ka ma haka ba mu ba wllh" Daren ranan Daddy ya iso daga Abuja, bayan ya huta suka d'an taba hira da Mama Hadiza da yake a part din ta sauka, sannan ya fita don xuwa ya gaida Inna, Imaan ta bi bayansa da sauri, bayan sun sauka balcony yana kallonta yyi murmushi saboda yasan akwai abinda take son gaya masa kenan tunda ta biyosa, yace "Do you need anything Imaan..." A hankali tace "Daddy kaga mutane sun yi yawa a gidan nan plss ni dai ina son xuwa gidan gwaggwo in xauna har a gama biki in dawo Saturday" Da mamaki yace "Bikin yayan naki kuma Imaan?" Tace "Daddy I will be very uncomfortable, ai da rana xan wuce gidan gwaggwo din ba da safe ba" Yace "Toh ita kuma Maryam fa, won't she be lonely" Imaan tayi dariya tace "Ae tare xa mu je daddy, ita ma tace min she's already uncomfortable tun daga jiya da mutane ke ta xuwa" Murmushi Daddy yyi yace "Ohk then sai ki gaya ma Ammin ki" Imaan ta wara ido cike da jin dadi tace "Toh Daddy nagode sosai, ai dama Ammi...." Shiru tayi hango Mujaheed da ta yi yana tahowa daga part dinsu, Daddy ya kalli inda take kallo, ganinsa ya tsaya har ya iso inda suke, da ladabi Mujaheed ya gaida Daddy, daddy ya amsa yace "Ya shirye shirye M.A" Murmushi kawai Mujaheed yayi, Imaan tayi wucewarta gaba ta bar su tana cinno baki, da sallama ta shiga parlon inna, Ta Rasulu na xaune kan darduma ta daura kafa daya kan daya ta rungume hannu tana sakace hakori, Inna kuma na xaune kan tabarma ita ma ta daura kafa daya kan daya, Umma na parlon xaune ga bucket cike da cin cin da alkaki da ta shigo da sai kallon ta Rasulu take kasa kasa, Ta Rasulu ta kyabe baki tace "Yo ai duk matsiyata ne Asabe, ni shi sa ba ruwana da kowa wllh, ba ruwana" Inna tace "A'a dama fa nasan a wajensu tsiya ya kare, ni ina ruwana da su Ina ta kai na, oh oh wlh" Ta Rasulu ta kalli Imaan sannan ta kalli Inna tace "Matar nan na amfani da iccen da kika bata kuwa?" Inna xata yi magana Daddy ya shigo da sallama Mujaheed na biye da shi a baya, Inna tace "Allah dai ya baku lada wannan hidima da kuke ta yi da Mujaheed, ko kudin jirgin da ka kashe yau ma ai xaune yake da kansa, Allah dai yasa ya ji k'an ku nan gaba, yayi ma imaan abun kirki ranan bikinta" Daddy ya xauna yana murmushi ya gaisheta sannan ya gaida Ta Rasulu, Umma ta gaishe sa sama sama, ya amsa yana tambayarta taro, ta Rasulu ta rike ha6a tana kallon Daddy tace "Ohh Bukari kana nan dama, rabona da kai fa tun da ka xo daurin auren ishaq" Daddy yace "Ina nan Baaba, sai dai yanxu a Abuja nake" Ta Rasulu tace "Toh Allah yayi maku albarka, ya kare ku sharrin masu sharri, ya sa ku gama lafiya da mu, ya ba matanku ikon yi mana biyayya yanda ya kamata" Yana murmushi yace "Ameen Baaba" Mujaheed ya gaida ta Rasulu, ta Rasulu tace "Sannu ango, amma kuma duk naga ka rame baka cin abinci ne?" Inna tace "Ke ma dai da wata magana ta Rasulu, ina xai ci abinci yana tunanina, kin xata rabuwa da ni abu ne mai sauki?" Dariya Daddy yayi yana kallon Mujaheed, Mujaheed ya kalli Inna ta gefen ido bai dai ce komai ba, Umma ta wani daure fuska tana hararan Inna ta gefen ido, Ta Rasulu tace "Toh kayi hakuri Mujaheed, abinda bayan bikin da sati daya kawai sai ka xo ka dauketa ka mayar da ita gidan naka gaba daya, ohh sa6o turken Wawa" Inna tace "Ae shine na ga, nayi kokarin fahimtar da shi hakan amma ya kasa kwantar da hankalinsa, sai in koma can gaba daya Imaan kuma ta dinga xuwa duk Juma'ah ta koma lahadi" Daddy dai sai murmushi yake, Imaan ta saci kallon Mujaheed taga kallonta yake, dauke kai tayi da sauri, Inna tace "Toh ni dai ta Rasulu ga ki ga Bukar yau, sai ki masa bayanin mutumin nan na bayan tsauni a tsanake, tunda ni na kasa fahimtar da shi da Ahmadu suna ganin kamar ko boka ne, Ni ko me xai kai mu gun boka mu masu tsoron Allah" ta Rasulu tace "Wllh Bukar ku maida hankalin ku don sai anyi da gaske da 'yar nan taka Imaan, tana da makiya ne ba na wasa ba, sannan wannan ciwace ciwacen nata ma ance ba banxa ba da sa hannu, sai an tashi tsaye kyam kada a kai mu a baro, bangaren aure kuma ance xata auri wanda ke bala'in sonta, wasu xa su yi murna da auren wasu kuma bakin ciki da hassada baxai bari su yi ba, wasu kuma takaici baxai yarda su yi murna ba, sannan da matsalaloli iri iri a xaman auren, matsaloli masu girma ba dadin ji kuwa, ni dai ba fata nake ba amma gaskiya abun ba dadin ji, kuma ance sai ta cika maka parlor da jikoki, toh ni abinda ban gane a nan ba shine... Kyashin fidda kudi kake a nema ma tillon yar ka lafiya ko kuwa kudin ne baka da shi Bukar?" inna tace "A'a sai dai kyashi, amma yana da shi wllh, Toh wllh sai ma kin tafi bayan biki xa su xo su sameni shi da d'an uwan suce in rabu da ke ba hanyar kirki kike nuna min ba, Toh wai dama Allah ba yace mu tashi ya taimake mu ba??" Daddy ya kasa daga kai, ta rasulu ta saki salati tana tafe hannu tace "Sai su ce ki rabu da ni kuma?" Inna tace "Wllh kuwa tatas xa su min suce in raba kaina da ke, ai ga shi nan xaune da ransa ba sharri na masa ba kullum na kawo masu xancen sai su gwaleni suce karya ce inyi ta kaina, to ni ya xan yi da su??" Mujaheed ya sunkuyar da kai sai murmushi yake, imaan ta boye fuska bayan kujera tana dariya kasa kasa, Daddy dai ya kasa dago kai, Ta rasulu tace "Dago kanka ka kalle ni Bukar, wllh wannan 'yar taka idan ba a tashi tsaye kanta ba duk sai mun shiga uku a duniyan nan, idan ma xaka fiddo kudi ka fiddo kudi a nema mata magani ta xama mutum, tunda har kuka iya karyata ni kai da Ahmadu to xa ku iya karyata Asabe ma" Inna tace "Yo na nawa kuma? Ai sun ma karya ta ni, sai dai Allah ya shirye su, ni dai na yafe masu" Daddy dai kansa na kasa, Ta Rasulu tace "Yanxu bayan biki sai ka ba Asabe dubu dari, idan ma ya kama muje tare da ita da Imaan din ne sai duk mu tafi...." Inna tace "Haba sai kace xa ki cuce ni, ai kawai ki je ke daya ba komai wllh" Daddy yace "Toh Allah ya kai mu xa a bada" Mikewa yayi yace "Na gaisheku xan je in huta" a tare suka hada baki wajen cewa "Toh Allah maka albarka" yace "Ameen" sannan ya fita parlon yana girgixa kansa. Umma da duk ta hada xufa gaba daya jikinta tana murmushin karfin hali tace "Toh Inna ayi hakuri da wannan din don Allah, ni xan koma in ji da baki" Inna tace "Toh ai ya fi babu, Allah dai yayi albarka" tana murmushi tace "Ameen" ta fice parlon da sauri tana share xufar goshinta a ranta kuwa hamdala take da Allah ya bayyana mata Ta Rasulu. Washegari Thursday duk yan matan gidan na ta shirye shiryen fita saloon da yin lalle, ita dai Imaan sai kumbure kumbure take... *Imaan isn't for free* it's 300 via Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah Then u show ur evidence of payment via my WhatsApp number 07087865788Mujaheed na dinning a xaune Maryam ta sakko downstairs tare da Maimoon, yana kallonta yace "Maryam" ta kalli direction din sannan ta tafi tace "Sai yanxu kake breakfast?" Yace "Ehh... xauna" ba musu ta ja kujera ta xauna, ya ajiye cup din coffee dake hannunsa yace "When did she tell you is the birthday?" Maryam ta langwabar da kai tace "She told me nothing about it again, tun ranan bata gaya min komai ba" Yana kallonta da kyau yace "Karya kike Maryam" ta xaro ido tace "Karya kuma ya M.A, bana ma tunanin Birthday din na nan don bata ce min komai ba, kuma kaga gashi ana ta hidiman biki, kila ma ta manta idan ma Birthday din na nan" yace "Make me a promise Maryam" tace "What promise" yace "You will watch her movement keenly" dariya tayi tace "Ohk then, amma kuma abun mamaki ina ma xata je ana biki" Yace "Just do what I say" tace "Toh na ji" yace "Good tashi ki tafi" Mikewa tayi ta bar dinning din, ya dau coffee dinsa ya ci gaba da sha a hankali. A bedroom Maryam ta tadda Imaan dake ta shiryawa slowly wai don a tafi a mance da ita, Maryam tace "Naga alamar baki son xuwa saloon din nan imaan" kamar xata yi kuka tace "That's just it, ni scalp dina ma ciwo yake min, aje ayi ta ja min gashi kaina ya fara min ciwo, ni dai kawai ku tafi kice masu baki gan ni ba" Maryam tayi dariya tace "Kai Imaan, da ni ke da irin gashin ki ai duk sati sai naje saloon" ita dai Imaan bata ce komai ba, Sadeeq ne ya fado mata ta tuna wata rana da daddare suna waya yake ce mata shi dai yana son dogon gashi, haka kawai taji tana ma son xuwa saloon din, Maryam ta gama yafa karamin veil din abayar jikinta tace "Ohk then xan ce masu ni ban gan ki ba" Imaan tace "Ko kuma ma dai kawai bari mu je, idan ya so ana gama mana sai mu tafi mu siya abinda xa mu siya a shopping mall, koh?" Maryam ta wara ido kamar baxata ce komai ba sai kuma tace "Ehh haka ne kuma" Imaan tace "Kinsan fa gobe ne birthday din kuma I have to give him the gift this night" Maryam tace "Au haba, same day da bikin Ya Mujaheed kenan?" Imaan tace "Sure" Maryam tace "Tabdi, Toh yanxu ya xa ki yi? Ga biki ga birthday" Imaan tayi yar dariya tace "Ni ina ruwana da biki, Ai na riga na ce ma Daddy xan je gidan Gwaggwon Ammina gobe da safe" Maryam ta marairaice tace "Tafiya xa kiyi ki bar ni yanxu?" Imaan tace "Of course no, tare xa mu ai" Maryam ta langwabar da kai tace "Yanxu haka xa mu yi missing bikin ya MA, gashi ma anjima da daddare xa ayi dinner fa" Imaan tace "Aa idan kinga xaki tsaya ki tsaya ni dai ba ruwana" Maryam tayi murmushi tace "Aa mu je gidan grandma din dai..." Imaan tace "Better" a tare suka fita dakin, Ammi dake parlor ta nuna ma Imaan kan kujera tace "Ga kayan ku nan ki shiga da shi ciki yanxu aka kawo" Imaan ta dauko ta kai daki sannan ta fito, sosai gaban Imaan ya fadi ganin Mujaheed parking space a tsaye, tun da ya kalleta sau daya ya ci gaba da danna wayarsa, ta dauke kai ta isa gun motar da ake kai su makaranta tana kallon Maimoon, Maryam kuma ta tafi gun Mujaheed tana murmushi tace "Our handsome groom..." Imaan ta tabe baki tana kallon Maimoon tace "Ina Drivern da xai kai mu Saloon din?" Maimoon tace "Ya Mujaheed yace xai ajiye mu shima fita xai yi yanxu" Xaro ido imaan tayi tana kallonta, ta hade rai bata dai ce komai ba, Ummi ta fito bangarensu tana kallon Mujaheed tace "Rahma xata taho daga baya, wai xa su fita tare da Umma yanxu" bude driver seat Mujaheed yyi ya shiga yana kallon Maryam yace "Har da ke xa aje gyaran gashin?" Ta xaro ido tace "Eh mana" murmushi yayi yace "Toh shiga..." imaan ta bi bayan Maimoon tana cika tana batsewa ta shiga back seat, Ummi ma ta shiga. Suna isa saloon din yyi parking yana kallon Maimoon ta madubi yace "Since babu mutane sosai a saloon din xan jira ku gama" Maimoon ta washe baki tace "Tohh mun gode Ya Mujaheed" a fusace imaan ta fice a motar ta bar door din a bude cikin tsawa yace "Keee" juyowa tayi da sauri, fuska daure yace "Xo ki rufe min mota kada in sauka in xane ki yanxu" Ganin babu wasa tattare da shi ta dawo kamar xata yi kuka ta rufe motar ta juya ta shiga saloon din, Maryam tayi murmushi tace "Ya M.A kai dai kawai kayi tafiyarka ko motorcycle din nan mai kafa uku sai mu hau ya dawo da mu gida" Mujaheed yace "Sauka kije kiyi abinda ya kawo ki nan" Yar dariyar yake tayi ta bude motar ta fita, ita kanta bata ji dadin jiransu da yace xai yi ba, shikenan ya ruguje masu plan. gyara ma Imaan gashi ake amma gaba daya hankalinta na gun lekan waje don ganin ko Mujaheed ya canxa mind dinsa ya tafi, amma duk ta leka sai taga yana nan, ta ji kamar ta kurma ihu, a haka har aka gama masu gyaran gashin aka fara masu lalle a hannu, Maimoon ce ta fara fita bayan an gama masu, Ummi ma ta fita, Maryam na kallon Imaan a hankali tace "Kinga yayi spoiling plan dinmu ko, yanxu how are we going to get the gift?" Imaan ta rasa abinda xata ce mata, can Maryam tace "You know what, kawai mu koma gida, dama akwai few abubuwan da nace ma mum xan siya a Nigeria, muna isa gida yanxu xan amshi card dinta mu fita daga can ma sai in siya abubuwan da nace" Sosai hankalin imaan ya kwanta, ta d'an yi murmushi tace "Toh shikenan, har naji dadi" tashi Imaan tayi suka fita saloon din din Maimoon ta bada kudin kafin su fita, tun da suka fito Mujaheed ke kallonsu ta madubi har suka iso gun motar, ganin Ummi xaune a gaba Maryam ta shiga back seat tare da Imaan, tada motar yayi ya dau hanyar gida. Suna isa gida Mujaheed yayi parking ya kashe motar, Imaan ta fita ta dau hanyar apartment dinsu, ya gyada kai yana bin ta da ido ta madubi... Maryam tace "Mun gode ya M.A" bai amsa ta ba tayi wucewarta tana murmushi. Maryam na gaya ma mama Hadiza xata fita shopping ta hanata wai bayan biki sai su je, ba ynda Maryam ta iya ta koma dakin Imaan a sanyaye ta sanar mata abinda mamarta tace, imaan ta rasa yanda xata yi, Maryam tace "Toh ko mu bari kawai gobe da safe idan mun fita xa mu gidan grandma dinki sai mu shiga mu siya" a hankali Imaan tace "Noo yau ya kamata in basa, yau nake son in basa" Shiru Maryam tayi, can tace "Ba xa mu je dinner ba anjima, kawai mu jira sai mutane sun cika wajen sai in sulale da makullin motar Yaya Yusuf mu je mu dawo" Imaan ta xaro ido Tace "Ni fa ban yi niyyar xuwa dinner din ba wllh" Maryam tace "Ae ko gwara ki daura niyyar xuwa yanxu, don that's the only way out" Imaan tace "Toh shikenan" Ana idar da Magrib duk aka gama shirin tafiya wajen dinner, duk wannan abun Mujaheed na lura da su keenly, kuma yaki tafiya duk da yanda abokansa suka dinga takurasa su wuce saboda amarya har ta iso wajen, Maryam dai ta dinga bin Yusuf wai ya bata makullinsa tayi driving din, daga karshe dai babu yanda ya iya ya bata, da kyar imaan ta saka gyale a kan ankon su na Dinner da Daddy yayi masu gaba daya gidan, tayi kyau har ta gaji amma sai wani nonnokewa take abunka da ba sabon ba, Maryam ce tayi driving din nasu xuwa hall din da xa ayi dinner din.... Waje ya cika makil da masu kudi sai ruwan naira ake tun kan a fara komai, Fara'a gun umma ba a cewa komai, Inna na xaune tare da ta rasulu a table guda duk sun sha atamfar England an yafa gyale sun tsuke fuska suna kallon ikon Allah, Imaan na shigowa hall din tare da su Maryam ganin Inna da ta rasulu ta rufe fuskarta gyalen jikinta ta dinga ba66aka dariya, suka nemi waje suka xauna, kallon inda amarya da ango ke xaune tayi, taga Safeenah da tayi wani kyau irin na aljanu sai sheki gwalgwalan jikinta suke, kayan jikinta kam dama ba acewa komai, ta kalli Mujaheed da ya sa lafiyayyen farin gezna sai walkiya yake, hada ido suka yi da shi tayi saurin kauda kai, Imaan ta kalli Maryam tace "Ni dai xan koma gun su Inna kafin mu fita" bata jira cewar Maryam ba ta mike ta tafi gun su Inna Mujaheed ya bi ta da ido. *Imaan isn't for free* it's 300 via Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah Then u show ur evidence of payment via my WhatsApp number 07087865788Inna na kallon Imaan da ta xauna kusa da ita cike da damuwa tace "Toh ba gashi kin fito sak mutum ba yau kin sa gyale, amma da kullum da hijabi xulum xulum kamar matar ladani..." Ta rasulu dake ta bin jama'ah da kallo tace "Toh wai ni abinda na kasa ganewa a nan shine... uwar amaryar da danginta basu san kin xo nan bane ban ga an xo gaishe ki ba har yanxu, dubi fa yanda muke xaune kamar gantalallu marasu makabuli babu wanda ya bi ta kan mu, an san ke kika raini Mujaheed tun yana tsumma kuwa, Kai duniya dai ta lalace ni ta rasulu" Inna ta tabe baki tace "Shine nake ta kallon ikon Allah, sai yawo suke mana da gwalagwalai kamar barayi babu wanda ya xo ya durkusa nan yace Sannu Inna... ya taro? To Allah ya sanya alkhairi ya nuna mana na 'yan baya, shi kuma Mujaheed din dubi yanda ya wani yi tsamo tsamo da shi kusa da amaryar babu walwala kamar dai wanda aka tilasta ya xo casun..." Imaan tayi murmushi ta kalli Mujaheed sannan ta kalli Inna tace "Toh ke ina ruwanki..." Inna tace "A'a da ruwana mana, ni ba karamin aikina bane in tashi inje samesa yanxu in ji ko lafiya..." Ta rasulu tace "Maxa je ki, nima naga rashin walwalan yayi yawa sai yake kawai yake, kamar wanda aka ma dole, anya ma auren soyayya xai yi kuwa" Inna ta tabe baki ta mike tace "Toh wani ya rainan min shi da baxan sani ba idan yana cikin damuwa ko akasin haka, sarai nasan sa ciki da bai, da abinda ke damunsa a xuciyarsa xaman da yayi a nan" Kutsawa ta dinga yi cikin mutane wanda yaki matsawa dama hankadesa take tana cewa "Yau naga bala'i mutane an xo cin shinkafa da yar kaza kamar mayu, an ki bani hanya..." Kallonta aka dinga yi ana bata hanya tace "Banda jaraba ko wacce ta fiddo kayanta na karkashin akwati ta saka ta xo mana nan tana jiran shinkafa da salaq da kaza, ohh yunwa ta yi yawa a duniya" A haka har ta isa inda amarya da ango ke xaune, wata kawar amarya ce tsaye tana bada history din amarya sai wani yauki take tana jujjuya idanuwanta, cool music sai tashi yake mutane na mata tafi... sake baki Inna tayi tana kallon yarinyar, can dai ta karasa inda take tsaye ta d'an ta6o ta a kafada, gaba daya wa enda suka san Inna suka xaro ido suna kallon ikon Allah, juyowa budurwar tayi tana kallon inna murmushi dauke fuskarta, Inna ta matsa kusa da ita sosai murya can kasa tace "Wani tsinannan telan kika ba kayan ki ya lalata maki haka saboda rashin tsoron Allah, duk duwaiwuka a waje?" Ba karamin tsorata da girgixa Inna tayi ba tana xare ido jin muryarta ya kauraye makeken hall din gaba daya ta cikin speakers, Hall ya rikice da dariya, Mujaheed ya sunkuyar da kansa, Umma ta kasa motsi inda take tsaye sai hadiye abu take da kyar, Imaan ta hade kai da table tana dariya kasa kasa, su Maimoon ma suna ta dariya daga inda suke xaune, Aunty da Ammi da Mama Hadiza dama tagumi suka yi suna kallon Inna da tayi tsamo tsamo a gaban hall sai kallon jama'ah dake dariya take, gaba daya yan uwan amarya wani kallo suka dinga yi ma inna, ita kuwa mai bada history ta ji kamar ta nutse gashi an ki daina dariya a hall, Safeenah ta wani hade rai tana kallon Mujaheed tace "Haba Mujaheed dama gate pass din wa enda suka kamata da wanda basu kamata ba ku ka dinga raba ma suka shigo mana nan, dubi wannan tsohuwar me ya kawota nan ta ina ta samu pass din shigowa har xata kunyata aminiyata cikin mutane, kasan Yar gidan wacece ita kuwa??" Gently Mujaheed yace "Watch ur words..." A fusace tace "Don't tell me that Mujaheed, how dare the old woman insult my friend that way, yar gidan governor ce fa tsaye a wajen..." Calmly yace "Ko yar gidan uban wacece, ke kawarki ce, to ni kuma grandmum dita ce a kusa da ita, so you dare not look into my face and say nonsense about her" Wani kallo Safeenah ta dinga ma Inna da ta tabe baki cikin sanyin murya tace "Ba lafiya, dama ba a sirri a nan, daga magana kuma sai sipikoki su dauka su min terere...." Juyawa tayi ta kalli yarinyar da ta kasa cewa komai har sannan tace "Ki dai maida masa ya gyara maki ai kudi kika biya ya cuce ki ya maki wannan dinkin" daga haka ta bar wajen ta tafi gun Mujaheed, har sannan Safeenah bata daina bin ta da wani irin kallo ba har ta iso inda suke tana kallon Mujaheed tana washe baki tace "Wannan ce amaryar Mujaheed" Safeenah ta dauke kai fuska daure, Inna ta rike ha6a tace "Ikon Allah, Toh Allah ya bada xaman lafiya, ta dai sha gwalagwalai maa sha Allah" Hajiyan Marafa ce tsaye kan Umma tana bala'i a mugun fusace tana cewa "Haba Rukayya ke baki ga irin manyan mutanen da muke ba gate pass bane xa ku ba wannan tsohuwa mai wanke wanke ta shigo mana hall tana shirme tana kunyata mutane, kin san yar gidan wacece tsaye a wajen take magana kuwa?? reputation dina da na 'ya ta kuke son 6atawa ko meye hakan?" Umma dai sai hakuri take bata a rikice tana cewa "Wllh ban san wanda ya bata pass din ba, don Allah kiyi hakuri Hajiya, wllh ban san daga inda ta taho ba...." A mugun fusace Hajiyan Marafa tace "Toh maxa ki sa a fitar da ita daga hall din nan tun wuri kada ayi mummunan abu a nan, maxa a fita da ita kada in sa masu gadi su fitar min da ita ta tsiya" Umma sai cewa take kiyi hakuri Hajiya xa ta tafi yanxun nan kuwa, ae ba ku kadai ta kunyata ba har mu wllh, ban san wanda ya bata pass ta shigo ba ni ban ma santa ba, haka irin tsoffin nan suke idan suka ga ana taro su shigo cikin jama'ah" Hajiyan Marafa ta juya fuu ta wuce tana cewa "Maxa ta bar nan kada in sa masu gadi su ja ta su fitar..." Inna na kallon Mujaheed tace "Toh naga duk baka da walwala lafiya kuwa, ko baka ci abinci bne?" Ya girgixa kai yace "Ba komai, ki koma kiyi xaman ki" Inna tace "Toh madallah sai dai har yanxu mu dai babu abinci babu labarinsa, ga ta rasulu can ma sai hamma take" Tana magana ta dau tsadadden drink dake gabansu tace "Ko in dau wannan" yace "Dauka" dauka tayi tace "Toh shikenan, Allah dai yasa ba mai halin uwarka xaka auro mana ba dai" daga haka tayi wucewarta, Safeenah ta bi ta da wani harara tana kyabe baki, Umma ta rasa yanda xata yi ta fitar da Inna a hall din cikin lumana, duk ta rikice taje can taje nan, Inna na dawowa xuwa seat dinta ta dinga cewa mutane "To dai duk wanda ya ci abu yyi hakuri ya saka gwangwani ko kwalin a jakarsa kada mu bata masu waje da kazanta mu cuce su...." A haka har ta koma gunta, ta ajiye ma ta rasulu drink din daya ta ajiye daya gabanta tace "Ma rage xafi..." Ta dau drink din ta fara budewa, Inna ta xauna tace "Naje na samesa amma kinsan ko gaisheni amaryar bata yi ba, ni dai ban kulata ba, ba ruwana kada in kunyata kai na cikin jama'ah ga ni babba, taro yayi taro in je inyi magana in kunyata Mujaheed din ma gaba daya, bakina a leko na juyo na dawo ai ana tare...." Ta rasulu tace "Gwara da baki kulata ba kam, ki bari sai an kaita dakin nata ki shirya kije ki mata tatas ki gaya mata yanda kike da Mujaheed" Inna tace "Ehh dama ai dole in sanar mata wahalan da nayi da shi don ta gane matsayina a wajensa, ana kai ta da washegari dama Imaan xan ce ta rakani inje in karanta mata yanda muke da shi" Umma ce ta taho gun Inna da sauri tana haki tace "Inna yanxu aka kirani wai ruwa ya cika parlon ki sai kwararowa waje yake ga kofar a rufe, ko dai kin bar pampon bayan gidan ki a bude baki sani ba?" Inna ta mike ta rafka uban salati a rude tace "Hadiza ta cuce ni ita ta shiga bandakin karshe tayi fitsari, shikenan ruwa ya shanye min gida na shiga uku na lalace ni patuu, ga dukiyoyi irinsu kujeru, tv, gado carpet, fridge duk a ciki" ta rasulu dake xabga salatin ita ma ta mike tace "Na shiga uku ni ta rasulu, jakata na dakin nima har da kudi dubu biyu, yanxu me xan ce ma 'ya yana daga xuwa biki ambaliya ya rutsa da ni??" Umma tace "Toh bari in sa driver ya maxa ya maida ku gidan gaskiya, don ruwa aka ce duk ya cika tsakar gida" Ko sauraranta Inna bata yi ba ta fice da gudu tana cewa "Innalillahi wa inna ilaihi raji'una ambaliyan ruwa a gidana a kira min yan kwana kwana, ga gudunmawar dubu hamsin da Bulasawa ya bani a dakin...." ta rasulu na biye da ita a baya ita ma da gudu tana salati, Mama Hadiza da su Aunty na ganin Inna ta fita da gudu suka taho gun Umma dake tsaye suna tambayarta me ya faru, Umma tayi wani dariya tace "Wai fa kudin da xata yi liki ta mance a gida shine wannan saurin wai driver xai maida ta gida" Kasa cewa komai Mama Hadiza da su Aunty suka yi, Umma tace "Allah dai ya kyauta, lamarin Inna ae sai ita" daga haka ta wuce ta bar su wajen a tsaye, Imaan dai na xaune an barta da jakunkuna irin na tsofaffi, Maryam ce ta taho gun Imaan da sauri tace "Ke maimakon mu bi su Inna mu je mu yi abinda xa mu yi kika bari suka wuce" Imaan ta xaro ido tace "Ae kuwa, toh kawai mu yi kamar xa mu bi su da jakar su sai mu wuce" Maryam tace "Toh dauko mu tafi" Imaan ta dau jakar Inna ta mika ma Maryam na ta rasulu, kallon Mujaheed tayi taga idonsa na kansu, ta dauke kai tana xaro ido tace "Maryam kin san Yaya kallonmu yake" Maryam ta kallesa taga still kallonsu yake duk da liki da mutane suka taru wajen suke masa da Safeenah, Maryam ta koma ta xauna tace "He is suspecting us Seriously, kin san me xai faru?" Imaan ta girgixa kai, Safeenah ta bude jakarta ta ciro new note din naira dari dari tace "Gashi ki tafi kiyi masu spraying, kafin ki dawo na fita gun mota sai ki sameni da sauri, but before then Bari in canxa seat" Imaan ta nufi can gaban hall din hannunta rike da tulin kudin, su Maimoon, Ummi, Rahma da wasu kawayen Safeenah da yan uwanta da suka sha gold sai cashewa wa suke da wakar jarumar mata da ya cike hall din Lol.... Safeenah ma na tsaye tana rawa gently tana kallon Mujaheed with love, shi ko yana tsaye kamar statue yana jujjuya wayar hannunsa, dance floor din kuwa banda dubu dubu babu abinda xaka gani a kasa sae few five hundred notes, Imaan ta isa kusa da su ta ki yarda ta kallesa tana kallon Safeenah dake rawa ta fara mata likin a hankali, kallon cikin ido Safeenah ke mata haka kawai Imaan taji gabanta na faduwa bata sake yarda sun hada ido ba tana ci gaba da yi mata likin kudin, Bandir din dubu daddaya Mujaheed ya ciro ya nufi gun kanninsa da suka dage sai cashewa suke barin Maimoon, Ya fara manna masu da daddaya da daddaya, Safeenah ta bi sa da wani harara ganin kanninsa kawai yake lika ma, Imaan na lura da abinda tayi haka yasa taki lika mata kudin hannunta gaba daya ta koma gun su Maimoon ta fara masu likin, Mama Hadiza ta xo ita ma tana ma su Maimoon da Imaan likin kamar su kadai ne a wajen tana murmushi, facing din Imaan Mujaheed yyi yana kallonta ya fara xuba mata one thousand naira note din a hankali, kasa kallonsa ta yi kanta a kasa, can kuma a hankali ta fara lika masa na hannunta, Mama Hadiza ta juyo ta dinga xuba masu na hannunta ita ma, Aunty ma haka, da abokansa gaba daya da suka cika wajen lkci daya, Safeenah ta ji kmr ta nutse don ba kowa wajenta sae flowing gown din jikinta, duk aka koma ana ma Mujaheed da Imaan liki, Umma sai xare ido take tana kallon ikon Allah, kowa ya xo sai ya fara ma Imaan da Mujaheed liki kamar ita ce amaryar, don wasu ko noticing Safeenar ma basu yi ba balle su san ba ita suke ma likin ba, Imaan dai ta dawo amarya a wajen duk kunya ya isheta.... Sai da Mujaheed ya manna ma Imaan gaba daya note din hannunsa yana kallonta, ita dai sai kokarin barin wajen take amma saboda yanda aka kewayesu ta rasa hanyar fita, da kyar dai ta samu ta lallaba ta fita taron xuciyarta na bugawa, tana kallon inda Maryam ke xaune taga har ta fita, da sauri ta nufi door din fita hall din ta fice fittt, Maryam na ganinta ta dallo mata fitilar motar ya Yusuf, xata tafi gun motar taji an fixgota, ihu tayi a tsorace ta juya xuciyarta na bugawa..... *Imaan isn't for free* it's 300 via Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah Then u show ur evidence of payment via my WhatsApp number 07087865788 Afuwan for the late and short update, am not feeling too well... Thanks in anticipation for understanding.Imaan kamar xata yi kuka tace "Ya Yusuf dubi fa yanda ka ban tsoro...." Yusuf yace "Ehh gwara ki ji tsoron, ina xa ku je?" Turo baki tayi tace "Gida mana, mun gaji" yana kallonta da kyau yace "Karya kike yi, ban kuma san lkcn da kika fara karya ba, and I need not to remind you the consequence of lying Imaan" shiru Imaan tayi tana kallonsa, ya d'an hade rai yace "birthday din makaryacin saurayin ki xa ku tafi koh, ke kin san waye Sadeeq kuwa? Kin san irin mutanen da yake abota da? Kinsan abubuwan da xa su faru gun birthday din nan da kika kwallafa rai sai kin je, why all of a sudden kika canxa from the decent Imaan da muka sani kika dawo mara ji?" Fuska daure yayi mata tambayar, kamar xata yi kuka tace "Ni fa ba birthday nace xan je ba, ai ba yau bane birthday din, kuma I only want to get him a gift now coz I know I might not get it tomorrow, ban ce lallai sai na je birthday ba" Kallonta ya dinga yi ta sunkuyar da kai a sanyaye, wayarsa da yyi vibrate ya kalla yyi replying text din da ya shigo sannan ya tafi gun motarsa ta bi sa da kallo, Maryam ta langwabar da kai tana kallonsa, yace "Ke ce ke xugata koh Maryam?" Xaro ido tayi tace "I don't get you" yace "Idan ke baxa ki gaya mata gaskiya ba why encourage her??" Maryam tace "Is there anything wrong with her getting her bf a birthday gift, we are in a civilized world Yaya Yousuf...." Yana mata wani kallo yace "Bani makulli na" Mika masa makullin sa tayi ta fito daga motar, Imaan dai sai kallonsu take ta gefen ido, ya juya ya koma inda take yace "Koma ciki..." A hankali tace "Toh ni gida xan tafi..." Ya daure fuska yace "Koma ciki nace" turo baki tayi ta juya ta koma cikin hall din, Maryam ta wucesa rai bace ta koma cikin hall din ita ma, Imaan na shiga ta tafi inda suke xaune tana kallon Mujaheed dake kallonta ta xauna, Maryam ma ta xauna a fusace tace "Gaskiya guys din nan sun fiye takura mutane, haka suke da sa ido dama, I won't tolerate this shit assuming we are staying together with them" Imaan ta tabe baki tace "I don't even know what's their business with me, sun dameni wllh" Maryam tace "Kece kike nuna kina tsoronsu ai" Imaan kamar xata yi kuka tace "Toh ni yanxu ya xanyi plss?" Shiru Maryam tayi tana kokarin nema masu wani option din, Yusuf dai na xaune d'an nesa da su yana kallonsu lkci lkci, ana fara cin abinci Maryam ta mike ta tafi ta debo masu yar fried rice ta cika nama ta dawo tana kallon Imaan tace "Let eat" Imaan ta girgixa kai tace "Am not eating" Har aka tashi dinner din Imaan bata da walwala, gashi da ta kalli Mujaheed sai ta ga kallonta yake, Tasowa Yusuf yyi ya taho inda suke ya ajiye ma Maryam makulli yace "You two should wait for me..." Daga haka ya wuce, Maryam tayi tagumi murya can kasa tace "Amma gaskiya wa ennan mutanen mayu ne, may be they know what we are up to" Ita dai Imaan bata ce komai ba idonta na kan Safeenah dake tahowa tare da Mujaheed kawayenta na biye da su a baya, hada ido suka yi da ita Safeenah ta wani daure fuska, Imaan ta dauke kai hade da tabe baki, sai da taga sun fita hall din sannan ta mike Maryam ma ta mike tace "Kinga hararan da yarinyar ke maki kuwa, did you know her b4?" Imaan tace "I don't know her fa" fita waje suka yi xuwa gun motar ya Yusuf, Aunty na kallon Yusuf a haraba hall din tace "Ka ajiye Mama Hadiza da su Hajiya Lailah a gida Yusuf..." Yusuf ya d'an bude ido amma bai ce komai ba, da sauri Imaan ta dauke kai tana wani murmushi, xagawa yyi ya budu front seat yana kallonta yace "Xo ki shiga nan" ta d'an xaro ido tace "Ya Yusuf Maryam fa?" Yace "Xata shiga wani motar, bana son musu ki xo ki shiga" Maryam ta hararesa ta dauke kai, A hankali Imaan ta taka ta isa front seat din ta shiga, Mama Hadiza da kawayen Aunty biyu suka shiga back seat, ya shiga motar ya bar haraban hall din. Yana parking a compound Imaan bata ko kallesa ba ta bude motar ta fice xata wuce apartment dinsu ta ji muryar Inna bakin gate tana cewa "Iliya Ahmadun bai dawo ba har yanxu??" Mai gadi da ya bar gate bude ganin motoci har uku dake bin bayan motar Yusuf yace "Ehh bai dawo ba Baaba" Inna na hango Yusuf da ya fito daga mota da Mama Hadiza da kawayen Aunty ta fashe da matsanancin kuka, da sauri Mama Hadiza ta nufeta tace "Me ya faru Inna" cikin kuka tace "Me na ma Rukayya a duniyar nan xata saka min da haka, ni fa na yarje ma Ahmadu aurenta tun tana yar jagaliya, yar yagalgal tana yawo da kodadden zani da yagaggen Hijabi" Mama Hadiza tace "me ya faru" Inna ta sharen hawayenta bata tanka ta ba tana kallon ta rasulu tace "Mu je kawai" ta rasulu tace "Idan ma kika yarda Rukayya ta kwana gidan nan yau Allah ma sai yayi fushi da mu da bamu dau mataki ba, irin wannan cin mutunci da raini haka? Oh oh tun da uwata Mai salati ta haifeni ban taba gani ko jin labarin irinsa ba, waiii.... Ai wannan babban magana ce wllh, ko kotu aka kai kara ba karamin muhimmanci xa su ba maganar nan ba, kuma da kyar idan ba sai an yanke mata hukuncin kare rayuwarta a gidan yari ba" Inna tace "Toh kun ji dai, ke dai mu je kawai wanda ya ajiyeta a gidan xai dawo duk gidan uban da yaje ya same mu, casun kuma da bamu samu ganin yanda xa a kare ba Allah ya isa xa mu hadu gaban ubangiji...." Ta rasulu na biye da ita tace "Ke ma dai wllh, sai ma kin fada?? Ae wannan a rubuce yake Asabe, abinda ba yafewa xa mu yi ba" Mama Hadiza da su Hajiya Lailah dai suka bi su da kallo. Imaan na kokarin saka kayan baccinta bayan ta fito wanka aka bude kofar dakinta, Maryam ce ta shigo ta tsaya tana kallonta tana murmushi, da mamaki Imaan tace "Ina kika je tun daxu kowa ya dawo banda ke??" Maryam tace "Close ur eyes please" Imaan tayi shiru tana kallonta, Maryam ta hade rai tace "Toh ko inyi wucewata" Murmushi Imaan tayi don sai sannan ta lura da hannunta dake boye a bayanta, a hankali Imaan ta lumshe idonta tace "Toh na rufe" Maryam ta isa kusa da ita ta tsaya tace "Bude ki ga gift da xa ki ba Sadeeq din ki" da sauri Imaan ta bude idon taga wani flower mai kyan bala'i da cards Maryam na mika mata tana jujjuya eye balls dinta, Imaan ta saki baki tace "What's this?" Maryam tace "Gift din da xa ki ba sa mana" Dariya Imaan tayi tace "You are very funny wllh, me xai yi da wannan din" Maryam ta xaro ido tace "Me xai yi da shi fa kika ce?matsalar ku kenan yan Nigeria wllh, ke kinsan Value din abun nan dake hannuna kuwa, kin san mu a turai wannan ya fiye mana kudi da wasu abubuwan rayuwa idan aka xo fannin kyautatawa, wllh I am telling you this sai ya fi son wannan akan kudin da xaki basa ko abinda xa ki siya masa, idan kin basa kudi me xai yi da shi bayan yana da fiye da wanda xaki basa, sai dai ma ya bada kudin kyauta tun bai shiga gida ba, idan kika ce xaki siya masa abu me xai yi da shi bayan bai fi karfinsa ba?? Wannan kam kina basa am telling you xa ki ga reaction dinsa..." Tana murmushi ta kare maganar, Imaan dai sai kallonta take nan kuwa a xuciyarta tunani take kuma fa gaskiyan Maryam tunda shi ma a turan ya taso xai so gift din sosai, Maryam ta kai mata flower din hancinta tace "Smell it" lumshe ido Imaan tayi jin wani cool scent da flower din yake, ta amsa tana murmushi tace "It smells nice, I love you Maryam" ajiye flowers din da card tayi gefen gado ta rungume ta. Umma na dawowa daga hall din dinner tare da kawayenta bayan sun sallami mutane gaba daya dama bata yarda ta shiga gidan ba, kawayenta su Hajiya Saude ne kadai suka shiga cikin gidan tunda haka dama suka shirya tun a hanya, Umma ta dau wayarta ta nemo lambar daddy tayi dialing, ba a dau lkci ba ya daga, tayi kasa da murya ta gaishesa ya amsa yace "Lafiya dai koh Hajiya Rukayya" Tana yake tace "Lafiya Baban Imaan, nace kana gida kuwa?" Daddy yace "Ehh na kusa gidan yanxu, driving nake" Umma tace "Toh Ina ma kofar gida, xan jira ka iso" yace "Ohk" daga haka ya katse wayar, Daddy na shigowa layin ya hangota tsaye d'an nesa da gate din gidan, parking yayi kusa da gidan ya fito yana kallonta yace "Lafiya kuwa?" Tace "Toh lafiyar kenan dai..." Yace "Mu shiga ciki toh" da sauri tace "A'a bari dai in maka bayanin a nan" Ya rungume hannunsa yana kallonta yace "Toh ina ji" Tace "Wllh Baban Imaan daxu ne Inna taje wajen da ake dinner...." Da mamaki Daddy yace "Yanxu sai da taje dinner din nan duk abinda muka gaya mata??" Umma ta bude hannu alamar ai shine, tace "Kuma da aminyar nan tata Baaba ta rasulu, wllh Abban Imaan sai kaga abinda taje ta dinga yi" Daddy ya girgixa kai yana kallonta, Umma tace "Wata kawar amarya na tsaye gaban jama'ah tana bada tarihin amarya in gaya maka sai Inna ta tafi ta sami yarinyar ya amshe microphone ta fara xaginta wai wani tsinannen tela ta ba kudi ya mata dinki, Kai maganganu dai babu dadin ji Abban imaan, ai su Mama Hadiza da Hajiya Aisha na wajen ni ba sharri na mata ba, wllh kunya kamar in nutse, dama imu imu ne abun xai xo da sauki amma fa ga dangin amarya sun cika wajen kuma Yan babban gida, bayan ta gama da yarinya mai bada tarihi ta tafi ta kwashe duk abinda aka ajiye ma amarya da ango a gabansu ta wuce ta bar wajen sirara, haka ta dinga ma mutane fada wai kada a xubda datti sun xo cin shinkafa da miya da kaza mayunwata kawai, maganganu dai ga su nan xar kayan kunya xar takaici Abban Imaan, yanxu fisabilillahi hakan ya dace?" Girgixa kai kawai daddy ya dinga yi yana salati, Umma tace "Toh ganin abun sai gaba yake sai naje na sameta nace toh fa ga ruwa can ya cike parlonta ta bar pampon bandaki a bude, shine Inna ta bar wajen ba shiri da kawarta Baaba ta rasulu, yanxu nayi laifi a nan Abban Imaan?" Daddy yace "Aa dai dai kenan" Umma tace "Toh nasan yanxu suna can kila ma ta tara jama'ah ana jirana, kuma ko me xata gaya ma Abbansu Mujaheed wllh yarda xai yi ya xauna a kai, shi sa ma nace bari in maka bayani tukun" daddy ya sauke ajiyar xuciya yace "Toh Allah ya kyauta, kuma hakan da kika yi shine dai dai, don da ba don haka ba baxa su bar wajen ba, kada ki damu nasan abinda xan yi, kiyi wucewar ki ciki" Umma ta d'an yi murmushi tace "Toh ngd Abban Imaan da ka fahimce ni" cikin gidan ya nufa ta bi bayansa bayan ta sauke boyayyen ajiyar xuciya. Inna ce xaune parlonta kan tabarma ta daura kafa daya kan daya fuskarta shabe shabe da hawaye tana fyace majina da hankicin hannunta, ta rasulu dake xaune kan darduma ta girgixa kai kamar xata saki kuka tace "Ni Ahmadu babu abinda ya fi min ciwo irin yanda muka dinga yawo muna xaga garin kaduna a adaidaita sahu muna neman wajen casu bayan mun dawo mun ga karya Rukayya take, daga karshe sai dawowa gida muka yi bamu gane wajen ba, mai adaidaita na bala'i mu ma muna bala'i, haka muka yi asaran dari biyun mu don da kyar mai adaidaitan ya amshi dari biyun wai sai dari shidda xa mu basa, wllh mune har sabon kawo neman wajen casu, babu wajen casu babu labarinsa" Mujaheed dai na xaune parlon sai kallonsu yake, Yusuf ma haka, Aunty da Ammi da Mama Hadiza ma duk suna xaune, Abba dai kansa na sunkuye yana sauraronsu, Cikin kuka Inna tace "Duk a kanmu sanyin daren yau ya kare muna yawo a daidaita neman wajen casu kaman yan iska, kuma ace inyi hakuri saboda ba a san ciwo na ba, ni wllh yau duk sai mu tattara mu tafi Police station, wacece kuma Rukayya da xata min wannan toxarcin, me aka yi aka yi ta, Rukayyar banxa Rukayyar hofi, ni dai wllh Ahmadu na xuba ido yanxun nan in ga matakin da xaka dauka kan katuwar nan, bikin ma ni sai in iya cewa a dage sai an bi min hakkina da na Aminiyata ta rasulu tukun, shkkn haka aka kare casun yau banda mu, ba mu ci Yar shinkafa da kazar da aka raba ba" sai kuma ta fashe da matsanancin kuka, Yusuf ya sunkuyar da kai yana murmushi, Ta rasulu na matsar kwallan da ya cika idonta tace "Ni wllh Asiya bata isa ta min haka ba, don sai dai in sa Muhammadu ya xabi ko ni ko ita...." Sallama aka yi bakin kofa, Inna ta amsa cikin rawar murya tace "Bukar yau dai bamu samu casun bikin Mujaheed ba, Rukayya dai yar iska ce wllh" *Thanks for the prayers via phone calls and WhatsApp messages fans, Allah bar xumunci, nagode sosai, am feeling a little better in sha Allah* *Imaan isn't for free* it's 300 via Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah Then u show ur evidence of payment via my WhatsApp number 07087865788Shigowa Daddy yayi parlon yana bin dukansu da kallo, Mujaheed ya mike ya koma kusa da Yusuf, Daddy ya xauna yana kallon Inna yace "Lafiya? Me ke faruwa?" Inna ta fyace majina a hankali tace "Kana ji Bukar? Bayan fitar ku daxu da yamma shine kawai na yanke shawarar tafiya wajen da ake casun ko minti sha biyar ne in yi in juyo duk da dai kun hanani, Toh ya xa ace bikin Mujaheed guda baxan je wajen casu ba, wllh Bukar mun shiga wajen da ake abun kenan mun xauna ko kayan kwalaman ba a fara rabawa ba sai ga Matar nan Rukayya tana haki wai in maxa in koma gida ance ruwa ya cika min daki da parlor, shine fa muka taho kamar mahaukata tare da Ta rasulu, muna shigowa gida in gaya maka sai muka ga bandaki a bushe tass babu ko digon ruwa balle ambaliyar ruwa, shine dai muka ta fada rai bace tare da Ta Rasulu nace mu koma wajen mu ji dalilin da ya sa xata gilla mana irin wannan karyar me tsada ko mu sa'annin uwarta ne, to fa muka dau adaidaita xa mu koma amma neman duniya mun wa wajen casun nan bamu gane ba haka muka ta walagigi a adaidaita sahu sanyin daren nan duk ya kare mana daga karshe muka dawo gida, yanxu fisabilillahi me na ma Rukayya xata min haka?" Daddy ya girgixa kai yace "Amma ba nace maki kada ki tafi wajen ba daxu da yamma Inna?" Inna tace "Bukar cewa fa nayi minti goma sha biyar kawai xan yi, ai da ban leka wajen ba wllh kullatata Mujaheed xai yi shi sa nace bari kawai in je a tsatstsaye in dawo, kuma meye laifina" Daddy yace "Haba Inna, yanxu fisabilillahi ki shirya ki shiga cikin yara ki xauna kice kin tafi wajen casu, me yasa kike mana haka don Allah?" Inna tace "Haba Bukar don dai minti sha biyar in juyo, wa ma xai san naje wajen banda mai sa ido? a baya fa muka xauna don ma kada a lura da mu" Daddy yace "Kwata kwata bai kamata, ban ga amfanin shiga cikin jikokin ki wai kinje casu ba, mu dai idan mun gaya maki magana baki ji baki amfani da shi, bamu san ko kina da wasu masu gaya maki bane bayan mu, ni bana jin dadin hakan da kike yi, kullum ayi ta magana amma baki gyarawa Inna, abinda baki sani ba a nan shine har mu kina xubar mana da mutunci a idon duniya...." Shiru Inna tayi sai 'yan idanuwa, a hankali ta Rasulu tace "Wllh Bukar sai da nace mata mu hakura kar mu je amma Asabe taki saurarata....." Juyawa Inna tayi tana kallonta baki sake, can ta kalli Daddy tace "Kaga xata gilla min sharri da rai na ko Bukar, to wllh ta ma riga ni shiryawa har tana cewa xata tafi ta bar ni ina bata mata lokaci, ni dai a dinga jin tsoron Allah ba ruwana" Ta rasulu tace "Yo idan ban ji tsoron Allah ba tsoron ki xan ji Asabe? Ke dai ki dinga bin 'ya yan ki sau da kafa baki da kamarsu, da Muhammadu ne yace min kada in tsallake ko nan da kofa wllh baxan tsallake ba, kawai ki sa mu shiga cikin jikokinmu mu xauna kamar wasu gantalallu har ana gilla mana karya don a kora mu...." Inna tace "Ni dai nace a dinga jin tsoron Allah ba ruwana, biki kuma gashi nan dai an gama sai kowa ya san na yi..." Ta Rasulu tace "Ina nan sai na raka Mujaheed gidansa na sa albarka...." Inna ta tabe baki tace "Toh naji na tafi casu ba da izinin ku ba Bukar, walakanta ni da Rukayya tayi fa??" Daddy yace "Ae ni na kirata nace ta fada maki haka saboda hakan kadai ke iya sawa ki dawo gida, don xuwan ki wajen bashi da fa'ida" Salati Inna ta saki tana kallonsa a hankali tace "Allah ya fi annabi sani...." Ta Rasulu tace "Toh ai da sauki tunda kai ne ka sa ta, kuma gaskiya da ba haka aka yi ma Asabe ba bata da ranan baro gun" Inna ta kalleta ta gefen ido ta rike ha6a tace "Ohh.. Naga abinda ya isheni, mutane dai basa tsoron Allah, da ranka ma sai an dinga bin ka da sharri" Mikewa Daddy yayi yace "Mu dai muna neman alfarmar ki dinga daukar maganar mu kina aiki da shi ba don mu ba don Allah..." Inna tayi kasa da murya tace "Toh ni dai kayi hakuri kuskure ne na riga nayi, sai dai Allah ya kyauta na gaba" Bai tanka ta ba ya fita parlon, Inna ta bi sa da kallo, Mikewa Abba yayi yace "Toh a dai yi hakuri inna" daga haka ya fita parlon shi ma ta bi sa da kallo, Mujaheed ya mike yace "Tsofe tsofe kice sai kin je casu..." Bai jira cewarta ba ya fice parlon yana murmushi ta bi sa da kallo, Yusuf ya mike ya fita parlon shi ma ta bi sa da kallo, Aunty dake kokarin danne dariyarta ta mike tace "Toh don Allah kuyi hakuri Inna" Inna ta tabe baki bata dai ce komai ba, Aunty tace "Bari in je Inna, muna aiki ne" daga haka ta fita, Ammi ma tayi mata sai da safe ta fita, tagumi inna tayi bayan duk sun fita tace "Lallai Bukar ya xama abun tsoro Ta Rasulu, ni da ba don a kan idona na haifosa ba ma sai ince canjin sa aka min a tsinannen asibitin turawan da na haifesa, ke kiji ashe shi yasa katuwar mata ta kirani ta gilla min karya, duniya ta lalace ni patuu" Ta Rasulu tace "Ai yanxu darajar sa Rukayya xata ci baxa mu daukaka kara ba, amma wllh bata ci bulus ba, ki kyale Yar iska Allah ya kai mu wayewan garin gobe lafiya" Inna tace "Shi kuma Bukar dama kada ya sake tako min nan tunda haka ya xama, ba ruwana ya je yyi ta kansa" Ta Rasulu tace "Atoh, ni da ace Salihu ne da na masa barbadin bala'i ynxu...." Mama Hadiza dai sai kallonsu take daga inda take xaune, Inna tace "A'a ni dai gwara da na bar figaggen da halinsa ba ruwana ace naje ina cecekuce da shi, gwara kawai da na masa shiru ya gama bambaminsa ya fita, ae shi Ahmadu baya haka, dama ni ban so ya shigo ba sai Ahmadu ya gama yanke hukunci, Toh sai gashi Allah ya jefo mana shi, haka kawai inje inyi magana bafillatanar matar sa ta ji haushi na ta kullace ni, A'a ba ruwana" Ta Rasulu tace "Dama shirun ya fi ina xaki tsaya cecekuce da d'an cikin ki?" Inna ta tabe baki tace "Ni dai ba ruwana, Allah ya shirye sa, amma Bukar gaskiya ba shi da hali duk cikin 'ya yana" Washegari tun da imaan ta tashi take jin xaxxabi da ciwon kafa, har karfe tara bata fito ba don ko Ina a gidan cike yake da jama'ah, Maryam dai tun da ta kawo mata breakfast dakin bata sake ganinta ba, Ammi ce ta shigo dakin karfe goma saura ganinta kwance ta karasa kusa da gadon tana kallonta tace "Lafiya?" Mikewa xaune tayi da kyar tace "Ammi kamar xanyi xaxxabi kuma kafana ciwo suke min" Ammi ta kai hannu jikinta ta ji da xafi, Juyawa tayi ta fita ta wuce kitchen ta hado mata wani shayin ta dawo tace "Kin ma yi wanka?" Kai ta gyada ma Ammi, Ammi ta mika mata shayin tace "Ki sha shayin sai ki sha drugs din ki" karba Imaan tayi ta fara Shan shayin Ammi ta dauko drugs dinta inda suke ta ballar mata bayan ta sha kusan rabin shayin Ammi ta mika mata maganin, Karba tayi ta sha Ammi tace "Ki tafi can bangaren Inna ki kwanta baki xa su sauka nan xuwa anjima kadan" Imaan ta xaro ido tace "Ammi bandakina fa?" Ammi tace "Ku dai ba ku da hali mai kyau abu dai na kwana daya, to sai ki kinkimi bandakin ki tafi da shi bangaren Inna ki ajiye" Imaan kamar xata yi kuka tace "Wllh bata ma mutum fa xa su yi, ni dai gwara in kulle in boye makullin" Ammi tace "Toh ki kulle tunda baki da hankali" Imaan bata ce komai ba Ammi ta juya ta fita, Mikewa tayi da kyar ta kwashe gaba daya kayan cosmetics dinta dake gaban madubi ta xuba su drawer, ta cire farin bedsheet dinta ta dau mai duhu ta shimfida tana turo baki, ta shiga bandaki ta dauke sabulu da sponge dinta sai brush da toothpaste ta dawo daki ta adana, hijab ta saka bayan ta dau sabbin kayanta na biki da xata saka a cikin leda ta fita dakin tana dingishi, babu yanda ta iya haka tayi ta gaida mutane har ta isa part din Inna, Ta Rasulu ce tsaye bakin kofa tana kallon tsofaffin da ke xaune cikin parlon tace "Don Allah ba don mu ba idan kun cire takalma a dinga ajiyewa a gefe guda kar su bata bakin kofar, bikin fa na yan gayu ne, haba takalma sai kace na masu talla" Imaan ta raba ta gefenta ta shiga parlon, daga kitchen Inna ya fito rike da cooler da plate ta duka tace "Toh ni dai basu gama girkin ba ina ji, wannan dai 'yar wainar da aka xubo min ne da safe sai in manna ma kowa guda biyu, ga miyar taushen mai kyau da nama...." Kallon Imaan dake gaida mutanen parlon xata wuce daki Inna tayi da sauri tace "Waye wannan kuma?" Juyowa Imaan tayi ta hade rai tana kallonta, Inna ta mike tace "Me xaki je ki min a daki??" Imaan ta marairaice tace "Inna baki suna dakina ne kuma bacci nake son yi" Inna tace "Naga abinda ya isheni, to Ina ruwanki da bakin Imaan? Gaskiya ni dai kiyi hakuri ki xo ki wuce na saka ma dakina turaren wuta kuma ma wannan mutumin...." Ko sauraranta Imaan bata yi ba ta shige dakin da sauri tana turo baki ta kulle, juyawa tayi, tayi still ganin Mujaheed kwance saman gado... Ta xaro ido tana kallonsa, A hankali Imaan ta bude kofar xata fita sai kuma ta juya tana kallonsa, Bude ido yyi yana kallonta shi ma, ta turo baki ta fita da sauri ta kulle kofar. Inna dake ta xuba waina a plate tana diga miya kamar xa a ba jarirai ta kalleta tace "Har kin fito knn, toh sai ki koma ki tambayar min shi ko in xuba masa wainar, tun safe yake nan ni dai ban ga ya ci komai ba, to rabuwa da ni haukane da xai daga hankali haka? Ni dai ba ruwana" Imaan xata fita Inna tace "Ji walakanci ina mata magana tana wucewa, baxa ki shiga ki tambayar min shi bane in je da kai na?" Dawowa tayi tana turo baki ta shiga dakin, Inna tayi tsaki tace "Babu abinda ta mance a halin ubanta mara kirki, nan ya wanke ni tass jiya da daddare, ni dai na yafe masa ba ruwana, ba don naka naka bane ai yanxu da sai dai in kora figaggiyar 'yar nan tasa ince ta fita, Toh kada laifin ubanta ya shafeta" Imaan na komawa dakin ta samesa idonsa rufe kamar daxu, ta d'an yi jim, can ta karasa kusa da gadon tace "Inna tace ta xubo maka wainar shinkafa?" shiru yyi har sannan bai bude idon ba, tace "Ka ji" nan ma bai ce komai ba, ta d'an ta6a kafarsa tace "Yaya ka ji?" Nan ma shiru kake ji, tabe baki tayi ta juya xata wuce ya fixgota ya bude manyan idanuwansa da suka sauya kala yace "Sai kin min ihu a kai saboda baki da hankali?" Shiru tayi tana kallonsa, can ta ta6a hannunsa ta durkusa kusa da shi a hankali tace "Baka da lafiya ne Yaya?" Mikewa xaune yyi ta dinga kallonsa, murya can kasa yace "Make me a cup of tea" Mikewa tayi ta nufi kofa ya bi ta da ido, Inna dake duke har sannan tana jiran ta fito tace "Xai ci ko in rabar ma tsofaffin nan?" Imaan tace "Shayi yace in kawo masa" bata jira me Inna xata ce ba ta shiga kitchen ta dau cup ta bude flask ta xuba ruwan xafi a cikin cup din sannan ta dawo tana kallon Inna tace "Ina Kayan shayin?" Inna tace "Wanda ke da shi ku ka siyo ku ka ajiye min kenan, toh kar ma ki bata lkcn ki ki koma bangarenku ki xuba masa kayan shayin a ruwan xafin nawa ya kusa karewa bbu wanda xan ba ma wllh" Wata tsohuwa dake xaune parlon tace "Haba Hajiya Asabe sai kace ba iyayensu ke siya maki ba?" Inna ta mike tana kallonta, can tace "Ehh lallai duniya ta lalace, toh wllh har na mance rabon da iyayensu su siya min kayan tea, sai dai yaron nan Bulasawa, kuma baya jiran wani ya kare yake kawo min wani, kawai mata tsohuwa baki san kan komai ba ki tsomo mana baki muna magana, ni dai ba ruwana a dinga jin tsoron Allah" Tuni imaan ta fice ta wuce part din su tana turo baki, Bedroom dinta ta fara shiga ta dau wayarta tayi dialing number Sadeeq, katsewa yyi ya kirata, a hankali tace "Good morning...." Yace "Morning my dear, hope kin tashi lafiya?" Imaan ta langwabar da kai tace "Sure, happy birthday once again..." Yana murmushi yace "Thanks much baby, I was so happy with ur text earlier this morning, naji dadi sosai baby" murmushi tayi tace "When xaka xo ka amshi gift din ka?" Yace "Ohh wai baxa ko xo party din ba?" A hankali tace "I might, I might not, kasan fa yau muna biki a gida.... But all the same ka dai xo ka fara amsar gift din ka" yace "Ni dai sai kin xo party din dear" murmushi tayi tace "Na ji" yace "Toh yaushe xan taho amsar gift din?" Tana juya ido tace "After Juma'at prayer" Yana murmushin sa mai kyau yace "Toh sai na xo baby" tace "Amma fa kar ka shigo layinmu, ka tsaya bakin titi xan fito" yace "Alryt dear xan kira ki idan na iso" tace "Tohm bye" daga haka ya katse wayar. Kitchen ta wuce don hada ma Mujaheed shayi, Ammi dake bayan kitchen din da Mama Hadiza suna magana tana kallon Imaan ta window tace "Me kike nema?" Imaan tace "Inna xan xuba ma kayan shayi nata ya kare" Ammi bata ce komai ba suka ci gaba da maganan su da Mama Hadiza, imaan ta hada shayi mai kauri ta rufe cup din ta fita, Ko kallon Inna bata yi ba ta shige cikin daki Inna na cewa "Ni dai dakina ya xama kamar kasuwa yau duk a tafi a bar ni da wari..." Ajiye shayin Imaan tayi tana kallonsa tace "Gashi yaya" ya bude ido ya mike xaune ta dau shayin ta mika masa tana kallonsa ya karba, makulli ya mika mata yace "Go to my bedroom and get me my phone" ta xaro ido tace "Ni kuma? A'a sai da in gaya ma Maimoon ta dauko sai ta bani, ni ba ruwana" Bai ce komai ba ya dinga sipping shayin a hankali, Mikewa Imaan tayi ta fita, tana fitowa parlon Inna ta kusa cin karo da Mama Hansai "Inna na ciki kuwa? Ga Ta Rasulu can tana fada da Hajiya Rukayya" Cewar Hansai kenan tana haki ta shige parlon Inna, Imaan dai tayi wucewarta, tsakar gida ta tadda ta Rasulu tsaye tana fadi Umma na fadi, Ta Rasulu na tafe hannu tana jujjuya ido tace "Nan nan aka auro ki kina raka yayarki Shafa tallan shinkafa da wake a kasuwar tasha, Hijabi duk a yakune, Zani duk duwaiwai a waje tsabar kodewa shine kin xo kin samu gida kin xama kamar buhun masara xaki kawo ma mutane raini toh wllh idan ban sa yarana mata sun nakada maki shegen dukar da xai fidda maki hakora uku ba kice ba Yar gidan mai salati bace ni, Ni nafi karfin ki wllh ni ba Asabe bace...." Muryar Inna suka ji tana sakin salati da karfi tace "Rukayya ita aminyar tawa ta Rasulu kike ma xagi ta uwa ta uba?? Ita ta rasulun kike kokarin dambe da?? La ila ha illallahu Muhammadur rasulillahi sallallahu alaihi wassalam, karshen duniya ta kama, ayi maxa a kira min Ahmadu amma banda Bukar...." Imaan ta girgixa kai tayi wucewarta ciki ta wuce sama, bude kofar dakin Mujaheed tayi ta shiga ta lumshe ido ta nufi saman gadonsa ta dau wayarsa, calls kusan ashirin yyi missing, yawanci kuma duk na Safeenah ne sai abokansa dake ta nemansa tun safe, ta tabe baki ta juya xata fita sai ga kira ya kara shigowa wayar, kallon screen din tayi ganin Safeenah ne tayi tsaki har ta isa kofa sai kuma ta daga ta kai kunne tayi shiru, daga daya bangaren Safeenah tace "Haba Mijina, tun asuba Ina ta kira no response are you okay?" imaan ta tabe baki tace "Toh ba shi bane" Da mamaki Safeenah tace "Wacece wannan?" Imaan tace "Kanwarsa ce, sai ki jira idan na kai masa wayar" bata jira cewarta ba ta katse kiran ta fito dakin ta kulle kofar. Ba karamin taro aka hada a tsakar gida ba Inna na ta ma Umma tijara Ta Rasulu na taya ta, ba abinda suka mance basu gaya mata ba, mutane sai bada hakuri suke, Ammi dama ko a gyalenta sai aikinta take, haka ma Mama Hadiza da ta ki fitowa, Aunty ce dai ta taho tana bada hakuri Inna ta tsigaleta ita ma ba shiri ta bar wajen, inna na ganin Imaan ta fixgota tana nuna ma jama'ah ita tace "Tana kamar haka fa Ahmadu ya aurota, amma yanxu ku dubi yanda ta koma kamar alade, Toh komai ta samu raruma take ta boye... ya ki halal ya ki Haram, duk ta tsiyace min d'a na... Shine kuma saboda abinci xata yi ma aminiyata rashin mutunci... Allah ya tsine ma abincin da xa aje a xaxxage a shata, tunda a kansa xaki xagar min Ta Rasulu, to wllh yau sai Ahmadu ya xaba ko ni ko ke a gidan nan ba ruwana, dama har yanxu ban huce casun da kika hanani ganin karshensa ba..." Umma dake ta kai koma ta kinkimo babban cooler din shinkafa da nama, da wani cooler din tuwo da na miya, da na fried rice da soyayyen kaji, da na masa duk ta dire masu a gabansu tace "Ni dai na xama kadangaren bakin tulu, ba kuma wani ya haifa min Mujaheed ba balle a nuna min iko da shi, Ikon ku ya tsaya iya Bukar da Ahmadu amma banda Mujaheed, abinci kuma ga shi aje ayi ta ci ayi kashi...." Ammi dake tsaye gefe ta taho har inda Umma take tace "ke dai a kwakwalwarki hauka ya kare, ita Innar kike fada ma magana haka saboda shinkafa" dakatar da ita umma tayi ta hanyar daga mata hannu tana mata matsiyacin kallo tace "Ni ban yi da juya ba, kije can ki ji da sauran ciwon da kika haifo duniya..." Aunty ta riko Ammi ganin finciko Umma xata yi, babban Jambox Hajiya Saude ta dauka ta kunna waka ya kauraye tsakar gidan kawayen Umma suka fito aka fara taka rawa irin na manya ana jujjuyawa, Umma na ganin haka ita ma ta shige cikin masu rawa ta fara takawa tana tafe hannu, Inna ta gwalo ido sai kuma ta fashe da matsanancin kuka tace "Ni kika xaga Rukayya?? Ni din??" Ta Rasulu ta dinga bude kulolin abincin tana ball da su duk abincin ya tarwatse a kasa, tana huci tace "Don kaza kazan ki dake da abincin kun ci kaza kazan ku...." Mama Hadiza ta fito daga part din su Imaan da sauri ta tafi ta dauke jambox din da waka ke tashi ta kashe sannan ta tarwatse sa a kasa tana kunduma ma Umma xagi tace "Idan kina tunanin uwata xa ki gaya ma magana yau ki xauna lafiya kin yi karya wllh, dama can ba son auren nan Mujaheed yake ba, ke ce ke son auren saboda abun duniya, xabin ki ce yarinyar ba tasa ba, kuma wllh wllh kin ji rantsuwar musulmi koh?? To baxa a daura auren nan ba, bari Ahmad din ya shigo.... in sha Allahu sai kin ji kunya yau, sai mun kunyata ki yau...." *Imaan isn't for free* it's 300 via Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah Then u show ur evidence of payment via my WhatsApp number 07087865788Shewa Umma tayi tana dariya tana ma Mama Hadiza wani kallo tace "Toh Sannu Uban Mujaheed.... Ahmadu, bari ki ji ko ita Mahaifiyar taku bata kai ta hana auren nan ba balle ke...." Mama Hadiza tace "Toh mu xuba da ke yau, wllh sai kin san kin yi da Inna, sai kin san kin taba uwar mu, xaman ki a gidan nan ya kare in sha Allah" Umma na ta rawa tace "Toh Ahmadu" Kujerun da aka jera a tsakar gida Inna ta dinga watsi dasu tana ball da su tana cewa "Kowa ya tafi gidan ubansa an fasa bikin, in dai da raina ni patuu baxa ayi auren nan ba, a kira min Ahmaduuuu..." Cikin daga murya ta Rasulu ma ke cewa "An fasa biki kowacce ta tattara ta koma inda ta fitoooo, Aisha ki kukkula masu shinkafar a leda su wuce, an fasa bikin...." Mama Hadiza da xuciyarta ke tafarfasa ta shiga kiran Abba da wayarta, yana dagawa tace "Ya Ahmad kana Ina? Ka dawo gida yanxun nan don Allah...." Abba yace "Lafiya?" Mama Hadiza tace "Ba lafiya ba, ka taho yanxu don Allah" bata jira cewarsa ba ta katse wayar, Yusuf da shigowarsa gidan kenan ya nufi Inna da mamaki ganin yanda take ta watsi da kujeru yace "Lafiya Inna?? me ke faruwa??" Inna ta fashe da matsanancin kuka tace "Isuhu xagi ta uwa ta uba Rukayya ta mana ni da ta Rasulu daga nace ta Rasulu taje ta amso mana abincin da xa mu raba ma bakin da ke parlona kada su tafi su ce an bar su da yunwa a bikin jikana, shkkn Rukayya ta dinga xagin ta Rasulu har ana rirriketa, da gudu Hansai ta xo ta sanar min shine na taho da sauri jin ba'asi, Toh wllh ni har xagin da ban san da shi ba a rayuwar nan sai da Rukayya ta min, har da ce min Ahmadu da Bukar kadai nake da iko da a duniyar nan, tana xagina tana xagin ta Rasulu, Aisha ta xo ta mata magana ta hada da ita, Hadiza ma ta xo yi mata magana ta hada da ita, Uwarka kadai ce munafuka wai ta xo tana ban hakuri maimakon ta taya ni kamar yanda Aisha tayi, Toh ni dai nace wllh an fasa daurin auren nan... yau dama naji labarin ita tayi masa xabin shegiyar yarinyar, to jiya a wajen casu ko gaisheni fa yarinyar bata yi ba sai kallon banxa ta min da lebbenta kamar gandan saniya" Yusuf ya kamo hannunta a hanki yace "Haba Inna, wannan ba girman ki bane, kiyi hakuri don Allah, gidan fa da baki don Allah kiyi hakuri ki bari....." buge masa hannu Inna tayi a fusace tace "Kaji min mutumin banxa ina ruwana da baki, ba suna kallo ake ci min mutunci ba sun taho sun tare min? Bakin banxa bakin hofi... To wllh kowa ya kama hanyar gidansu dama ba ruwana...." Gaba daya su Maimoon da Maryam dai na tsaye gefe sai kallon ikon Allah suke gida duk ya hautsine, kawayen umma da umma kuma basu fasa kunna Jambox suna ci gaba da taka rawa ba suna tafi, Ta rasulu ta tafi iya karfinta ta wangale gate cikin daga murya tana cewa "Ku fito ku tafi gidajen ku babu xancen biki jama'ahhh" Aunty ce ta dinga tambayar su Maimoon inda Mujaheed yake don tasan shi daya ke iya jan Inna ta bar tsakar gidan, Imaan dake tsaye sai hararan umma take, nan ko jira take ta kara gaya ma Inna magana ta rama mata, tana kallon Aunty tace "Yana can dakin Inna" Aunty tace "Yi maxa ki tafi ki kirasa kiyi sauri" Juyawa tayi ta wuce part din Inna tana rike da wayarsa har sannan, babu kowa parlon Inna duk mutanen ciki sun taho tsakar gida kallo, Ta bude kofar dakin ta shiga, Xaune ta samesa har sannan bai gama shan tea din hannunsa ba, ta hade rai tace "Yaya Aunty tace in kira ka...." Ya mata wani kallo yace "Did I ask you to announce I am here?" Turo baki tayi tace "Toh Inna ce da Baaba ta Rasulu ke fada a tsakar gida" Ya buda manyan idanuwansa yace "Fada kuma??" Ta gyada masa kai, yace "Da wa?" tace "Umma" shiru Mujaheed yyi, can ya girgixa kai ya ajiye cup din hannunsa ya mike ya fita, bin bayansa imaan tayi, Tun daga nisa Mujaheed ya tsaya ya dinga kallon crowd da aka tara a tsakar gida, ga sautin waka, ga muryar Inna, ga muryar ta Rasulu, abinda bbu dadin ji, imaan ta iso inda yake tsaye tace "Yaya kaje ka ma Inna magana" shi dai bai ce komai ba, can ya karasa wajen a hankali yana kallon Inna kafin yace komai ta rushe da kuka tace "Mujaheed wai ni yau Rukayya ta xage tass, Mujaheed ba abinda ta mance bata gaya min ba...." Yace "Toh mu je ciki a kira maki Abba yanxu, wayar na can bangaren ki" Bayani ta dinga masa tana kuka, yace "Nace mu je a kira Abba..." da haka Inna ta bisa tana kuka wiwi tana jera Allah ya isa ma umma, Ta Rasulu dai na can bakin gate tsaye ta wangale gate din tana ihun a xo a tafi gida an fasa biki, su Aunty suka dinga hada kujerun da aka tarwatsa tsakar gidan kowa dai rai ba dadi. Mujaheed ya dinga kallon Inna Bayan sun shiga parlonta, tayi kukanta mai isarta, Imaan dai na durkushe parlon ita ma tana kallonta, Inna ta hadiye kukan da take tana kallon bakin kofa ganin Tsofaffin da suka xo biki ne suka dawo mata tace "Yau naga abinda ya isheni.... ba an fasa bikin ba ku yi ta kanku ku koma gidajen 'ya yan ku mana bayin Allah...." Wata Yar tsohuwa tace "Ae bai kai ga haka ba Hajiya Asabe hakuri xa ki yi, tun da an fara abun nan a gama...." A fusace Inna tace "Toh duk ku koma tsakar gidan ku xauna a can, ni dai ba ni ke aurar da d'a ba ba ruwana, a rufe min kofa" sallama suka mata suka wuce ta mike ta kulle kofarta ta dawo tana kallon Mujaheed tace "Ka kira min Ahmadun?" Shi dai bai ce mata komai ba, a fusace tace "Wai baka ji na ne Mujaheed??" Yace "Ae sai ki saurara ki gani" tana fyace majina tace "Dama kada in kuskura in ga Bukar a parlon nan yau ba ruwana, kada ya xo min Ahmadu kawai nake bukata" Bata rufe baki ba sai ga Abba ya shigo da sallama tare da Daddy ko wannensu da wani expression yake kallonta, Inna ta tsuke fuska tace "Ni dai Ahmadu kadai na kira...." Abba ya xauna har sannan bai daina kallonta ba, Daddy dai bai ce komai ba ya xauna, sai ga Mama Hadiza ta shigo, Inna tace "A kira min Aisha da Amina ma su xo a akan idonsu aka yi komai ai" Mama Hadiza ta nemi waje ta xauna babu walwala tace "Suna xuwa" Aunty ce ta fara shigowa sannan Ammi duk suka xauna saman tabarma, Ta Rasulu ce ta shigo parlon tana kuka wiwi kamar yarinya ta wuce daki sai ga ta ta fito da 'yar jakarta tace "Asabe gidan nan ba gidan xama bane, ni tunda uwata Mai salati ta haifeni ba a ta6a min cin mutuncin da Rukayya ta min yau ba, Ina dalili ina Dan mafari ni sai yanxu wasu maganganun ke dawo min suna min ciwooo..." Mikewa Inna tayi ta rushe da kuka ta rike jakarta gamm tace "Ai babu inda xaki Ta Rasulu muna nan sai an bi mana hakkinmu....." Rungumeta ta Rasulu tayi nan suka dinga rusa kuka a tsaye, imaan ta boye fuskarta ta dinga dariya kasa kasa, Mujaheed kam sunkuyar da kansa yyi, Abba ma dai kansa na kasa, Daddy kuwa sai kallonsu yake, kuka mai isansu suka yi sannan suka saki juna, Inna ta maida jakar daki ta fito, Ta Rasulu ta xauna ta daura kafa daya kan daya ta tsuke fuska, Inna ta xauna tana kallon Abba tace "Toh Ahmadu yau dai sai ka xaba ko ni ko matarka Rukayya...." Sai a sannan Abba ya dago kai yana kallonta, Inna tayi mitsi mitsi da ido tace "Kuma aure na samu labarin xabinta ce yarinyar ba xabin Mujaheed ba don haka daurin aure ya fasu in dai ni na haife ku" Abba ya girgixa kai ya ma rasa abinda xai ce, daddy ya d'an sauke ajiyar xuciya gently yace "Amma me ya faru Inna? Meye musabbabin matsalar?" Wani kallo Inna ta jefa masa ta kankance ido tace "Dama wannan ya xama maganan ka ta farko kuma ta karshe a parlon nan, don ni ban san ma wa ya gayyato min kai ba, abinda ya faru kuwa shine yau har uwata dake kabari sai da Rukayya ta xaga a kan shegiyar shinkafa, har tana neman dunguri na, ga rawa da ta dinga yi a gabana tana min murgude murgude da kawayenta wai su fitsararrun yan tasha, daga fa mun je amso ma bakin mu da ta Rasulu shinkafa, xagi ta uwa ta uba dai yau mun sha sai godiyar Allah..." Girgixa kai kawai daddy yake yace "Ikon Allah" cikin rawar murya Inna tace "Toh ni yanxu na xuba ido in ga matsayina a wajen ku in ga matakin da xa ku dauko, ko kaffara baxan yi ba tun da Ahmadu yake ko kallon banxa bai taba ma Hadiza Uwar Rukayya ba, toh ni me na mata daga xuwa amsan shinkafan biki xata tsigaleni..." Sai kuma ta fashe da kuka mai ban tausayi tace "Me na ma Rukayya yau ta min cin mutunci wanda da wuya tabon ya goge a jikina" Ta Rasulu ta saki kukan ita ma tace "Me kuwa xa ki mata Asabe, ni ba don albarkacin ki ba nasan da yau sai 'ya yana sun turo motar sojoji an fitar da Rukayya gidan nan...." Inna ta dakatar da kukan da take da sauri tace "A'a yanxu ma bai baci ba Ta Rasulu, kira su su turo motar babu abinda ya sha min kai wacece kuma Rukayya ina ruwana da ita xata ci albarkaci na? Su kwasheta ba ruwana" Abba dai bai ce komai ba har sannan, can dai ya dau wayarsa ya shiga kiran layin umma, har ya gama ring ba a dauka ba, ya kalli Mujaheed da ke ta kallon inna yace "Tafi ka kira min uwar ka yanxu..." Mujaheed ya sunkuyar da kansa bai dai ce komai ba ya mike ya nufi kofa a sanyaye ya bude, karo ya kusa ci da umma dake labe tana sauraron komai, shi dai bai ce mata komai ba, har xai tsaya kawai yayi wucewarsa don bai ma son ransa ya kara baci, Sallama Umma tayi ta shiga parlon da lullubi kanta a kasa, Inna na ganinta ta saki salati tana tafe hannu tace "Almunafunfun kenan ku ke ga, to ai ba da gyale kika min cin mutunci a tsakar gida ba don haka sai ki cire ki ajiye a gefe a gama magana, kuma ni dai Allah ya isa rawan da kika dinga yi a gabana kina mokade mokaden maxaunai" Umma ta xauna nan kusa da kofa bata dai tanka ta ba, tana kallonsu Abba tace "Ga ni nan" Sai hararanta Mama Hadiza take, Abba na kallonta da kyau yace "Ita Innar kika xaga yau ko?" Ta Rasulu tace "Ta uwa ta uba kuwa, har ana rirriketa xata doketa, ni dai guduwa nayi na koma bakin gate, kawai 'ya yana su ji daga xuwa biki duka ya ritsa da ni" Abba na kallon Umma yace "Toh yayi kyau, ki tafi gidan ku yau, ko minti goma ban son ki kara a gidan nan...." Da sauri Inna tace "Aa baxa fa ta tafi da igiyar ka mai daraja ba tana galantoyi a titi, yanxun nan xaka datse shi ta tafi gidan nasu tsirara, sai kuma taje can ta dinga xagin uwarta mai ciwon kafa a kano..." Ta Rasulu tace "Ko ta koma wajen shafa mai shinkafa da wake a kasuwar tasha" Umma tace "Toh Alhmdllh xan tafi amma sai a barni in sallami bakina da suka xo biki ko xuwa da yamma" Inna ta mike tace "Wani biki? Bikin da aka fasa ko kuma wani daban kike nufi?" Kallonta umma tayi da sauri, Inna ta tabe baki tace "Ae babu xancen wannan auren, don baxa a ma jikana dole ba, maxa maxa a kira dangin shegun amaryar a sanar masu suyi hakuri Mujaheed yace ya fasa, in dai da raina wllh an fasa auren nan, ni ba ruwana" Abba yace "Bai kai ga haka ba Inna..." Katse da tayi tace "Ya kai har ya xarce Ahmadu" Daddy yace "Haba Inna, kananun mutane kike son ki maida mu, daurin aure nan da 'yan awanni kice a fasa???" Inna tace "Ba ruwana idan ma jarirai xan maida ku, daurin aure dai ni patuu nace bbu shi, idan kuma akwai wanda ya isa ya ja da ni to Bismillah...." Mama Hadiza sai gyada kai take don hka ya mata mugun dadi, a hankali Abba yace "Inna to bakin da suka xo daga garurruwa da dama don bikin fa? Ya xa mu yi da su?" Inna tace "Oho sai a nemi wata a daura auren da ita amma ba xabin Rukayya ba, babu kuma shegen da ya isa ya sa in canxa ra'ayi na gaskiya..." Ta Rasulu tana tabe baki tace "In har kuna son gamawa da Asabe lafiya ku bi abinda tace sau da kafa, jama'ah kuma da aka tara tunda abun kunya ku ke gudu sai a samo yarinya ko cikin 'yan uwana ne a daura auren kowa ya hutu" Inna tace "Shi kansa Mujaheed din ba son auren yake ba wllh wllh, idan kuma karya ne a kirasa a tambayesa a ji ta bakinsa, haka kawai xa a cutar min jika a masa auren dole abinda aka daina yayi tun lokacin kakata Furera...." Daddy yace "Toh gwara a kira Mujaheed din a fara jin ta bakinsa Inna...." Dakatar da shi Inna tayi tace "Ka karyata ubanka isuhu Bukar.... Kuma a kira Mujaheed din" babu Wanda yace mata komai a parlon, Umma dai tuni yan hanjinta suka kada ta fara matsar kwalla, idan aka ce an fasa auren nan da gaske ai an kasheta kenan balle ta san in sha Allahu sai anyi, cikin tsawa Inna tace "A kira Mujaheed din mana tun da karya nake" Mama Hadiza ce ta kira layin Mujaheed, yana dagawa tace "Ka taho parlon Inna yanxu" daga haka ta katse wayar, Inna dai sai girgixa kafa take, ba a dau lkci ba Mujaheed ya shigo parlon da sallama kansa a kasa, nan kusa da imaan dake xaune jikin kujera ya duka don babu waje parlon bai kuma son xama kan kujera, Inna na kallonsa tace "Tsakanin ka da Allah Mujaheed kana son auren yarinyar nan da Rukayya ke son hada ka da?" Shiru Mujaheed yyi yana kallonta, can ya saci kallon Umma dake kallonsa tana matsar kwalla, sunkuyar da kansa yayi, Inna tace "Kun ga munafuki koh??" Abba ya hade rai yace "Don't waste our time Mr Man" d'an murmushi yyi yana kallon Inna yace "Toh Inna da bana sonta ai baxan yarda da auren ba" Sake baki Mama Hadiza tayi tana kallonsa, Umma ta sauke boyayyen ajiyar xuciya, Inna ta saki salati tace "Jini ba wasa ba ni Asabe, Allah sarki Ahmadu kana cikin jarabawar ubangiji 'ya ya duk sun kwaso halin uwa...." Wani kallo Mujaheed ya dinga mata, Inna tace "Toh oho dai, da ka so yarinya da kar ka so ta duk uwasu daya ubansu daya, aure dai tunda aka xageni aka ci ma ni da aminiyata mutunci babu xancensa an fasa, sai dai duk abinda xai faru ya faru Babu kuma wanda ya isa ya canxa min ra'ayi ko waye shi kuwa, idan baku son a maku kallon kananun mutane kamar yanda ku ka ce sai a samu wata yarinyar a aura masa amma ba xabin Rukayya ba, xan nuna ma kowa ni jarababbiya ce yau" daga haka ta mike ta shige daki tana goge guntun hawayenta, Abba ya jinginar da kansa da kujera yana salati a ransa, Daddy kam sai girgixa kai yake ya rungume hannayensa, a hankali Imaan ta mike ta fita parlon Mujaheed ya bi ta da ido haka ma Abba da Daddy. *Imaan isn't for free* it's 300 via Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah Then u show ur evidence of payment via my WhatsApp number 07087865788Daddy na kallon ta Rasulu a hankali yace "Yanxu Baaba don Allah baxa ki bata hakuri a daura auren nan ba saboda mutanen da aka tara??" Ta Rasulu ta xaro ido ta mike tace "Toh Asabe ga Bukar nan wai in baki hakuri a daura auren... da yake dama cikin 'ya ya ma akwai mai gudun bacin ranka akwai kuma wanda bai san ciwon ka ba kwata kwata, toh Bukar dai bai san ciwon ki ba, don da ya sani sai in da karfinsa ya kare a shakiyancin da Rukayya ta mana yau" Daga haka ta shige daki murya can kasa tana cewa "Ba ruwana.... Haka kawai ince Asabe ta hakura ta ji haushi na..." Mama Hadiza na kallon su Abba on a serious note tace "Wllh Yaya tun da Inna tace baxa ayi auren nan ba fa baxa ayi ba, nima kuma dama nace baxa ayi din ba, ba kuma abinda xai sa ayi, sai an nuna ma Rukayya duk fitinar uwar mu a haka muke sonta kuma babu shegen da ya isa ya taka mana ita ya xauna lafiya, babu shi a duniya wllh, tun wuri ku kira dangin amaryar ku sanar masu an fasa don su san nayi, tunda uwata tace baxa ayi ba baxa ayi ba, ni nayi Imani da Allah da kun ji irin cin mutuncin da tayi ma Inna yau baxa ma ku tsaya kuna bin maganar a sanyi sanyi ba, kuna shakku a ran ku, me aka yi aka yi Rukayya xata raina mana uwa mu kasa daukan mataki?? to wllh yau sai ta ga iyakarta sai dai idan ban haifu ba...." Tana kai wa nan ta mike a fusace ta fice a parlon, Umma ta tabe baki ta dauke kai, Mikewa Daddy yayi ya fice daga parlon shi ma, a hankali Mujaheed ya mike ya bi bayansa, Abba ya kalli umma da kyau yace "Ki bar gidan nan as soon as possible Rukayya bana son ganin ki..." tace "Toh xan tafi ai dama ba sai ka maimaita ba yallabai, amma dai kar ka manta yar gidan wacece Mujaheed xai aura, tsaf xa ku xubar da mutuncin ku da kimar ku a idonsu, da ma duniya gaba daya, barin kai da kake sanannen Barrister" tana magana tana matsar kwalla, har xata fita sai kuma ta tafi kofar dakin Inna, Bude kofar tayi ta durkusa tana goge kwallan idonta tace "Ina neman gafaran ku inna, ku yafe ni ku yi hakuri sharrin shaidan ne..." Inna ta mike a rikice tace "Auzubillahi, garin yaya aka bar ta taxo min nan ni Asabe, don Allah ki rufa min asiri ki fita ba don hali na ba, ki tafi don Allah Rukayya" Mikewa Umma tayi ta fita parlon.... Abba da Daddy ne xaune parlon Abba duk sun rasa abun yi gashi har sha biyun rana ya kusa, fasa aure gaskiya is out of the point yanxu, bai kamata bane kwata kwata amma basu san ta inda xa su billo ma al'amarin ba, Mama Hadiza ce ta shigo parlon da sallama ta dalilin kiranta da Abba yyi, Ta nemi kujera ta xauna tana kallon yayyin nata, Murya can kasa Daddy yace "Yanxu Khadija baxa ki taimaka ki ma Inna magana ta janye wannan batu na fasa aure ba, da dai ace daga wajen mu aka fasa daurin auren nan gwara hakan ya faru daga bangaren iyayen amaryar.... Ki dubi irin mutunta gidan nan da ake amma aga irin haka ya billo daga gidan, ga mahaifin yarinyar dattijon kirki ga kuma irin manyan mutanen da xai gayyato daurin auren nan, kaninsa kuwa wajen aikinsu daya da Sadeeq kuma suna mutunci....." Mama Hadiza ta katse sa tace "Toh ko in ja Innar mu tafi gidansu amaryar tayi abinda xai sa daga wajen su suce sun fasa daurin auren tunda dama kowa kallo masifaffiya mara hakuri yake mata?" A fusace Abba yace "Ji wata maganar banxa, kina ma da hankali kuwa Hadiza?" Mama Hadiza ta mike tsam tace "Ehh kwarai Ina da hankali Yaya, dama naga take taken ku, wato ku baku ma wani ji haushin abinda aka ma mahaifiyar ku ba saboda fitinarta ko, infact ba ku ma yarda cewar ita ke da gaskiya ba, to wllh bari ku ji in har baxa ku bi abinda tace ba toh ku xa ku yi ta ganin ba dai dai ba, ba ruwana, sannan duk fitinarta xan dauketa daga gidan mu tafi sai ku xauna da matanku ku ci karanku ba babbaka, ita ma Rukayyar sai ka ce ta dawo masifaffiya ta tafi" daga haka Mama Hadiza ta fice daga parlon a fusace, Daddy ya girgiza kai yace "Bata da hankali kwata kwata" Abba ya sauke ajiyar xuciya yace "Ni fa nasan duk abinda Inna ta fada Rukayya xata iya aikatawa, kuma ko wani hukunci tace in yanke mata yayi dai dai, amma not to the extent da xata ce a fasa daurin aure ranan daurin aure, meye laifin iyayen amaryar? Ina ce Rukayya ce ta mata laifi ba su, gaskiya Inna tana son ta samu cikin wani yanayi ne, Innalillahi wa inna ilaihi raji'un..." Daddy da yyi shiru yana sauraren yayan nasa yace "Ko xaka kira Bala da su Jibril su mata magana?" Abba yace "Sai kace baka santa ba ai ni har yanxu ban ga wanda ya isa ya sa Inna ta canxa ra'ayin nan ba sai dai wani Ikon Allah" Abba ya jinginar da kansa jikin kujera yace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, where are we to start from coz gaskiya babu xancen fasa aure, duk hukuncin da tace ayi ma Rukayya xa ayi amma banda fasa aure don iyayen yarinya basu san hawa ba basu san sauka ba xa mu kunya ta su a idon duniya" Daddy ya tallabi chin dinsa thinking of a way out also. Karfe sha biyu Abba da Daddy da su kawu Bala da Jibril da wani kanin Inna da suke uba daya suka kara komawa bangaren Inna don su bata hakuri ta janye batun fasa auren Mujaheed da Safeenah, kora irin ta kare Inna ta masu da maficin hannunta, har kawu Bala na neman faduwa saboda saurin ya fita a parlonta, Inna ta rakosu har bakin pamponta tana huci tace "Munafukai kawai" Su dai basu juyo ba, amma daddy gaba daya ransa ya gama baci, Abba dai ne ke murmushin karfin hali, su Bala da Jibril ba bakin magana sai yan idanuwa, kanin Inna Alhaji Audu ne ya dinga cewa "Tun da muka fito lafiya Alhmdllh, Asabe ba kyau" Daddy na isa part dinsa ya shiga ko sallama bai masu ba, Imaan da Maryam na dinning xaune Imaan na bata labarin abinda ya faru parlon Inna kasa kasa, Mama Hadiza na daki tare da Ammi, Ammi ta fito jin an bude kofa ganin daddy ne tana kallonsa ta xauna saman kujera bata dai ce komai ba don Mama Hadiza fa na kan bakanta na cewa babu xancen daurin aure ranan har ta gama hada kayanta, Daddy ya jinginar da kansa da kujera yace "Inna na son bata sunan gidan nan ta kunyata mu a idon duniya ne kawai, ta mance cewa bayan Mujaheed akwai yan baya da xa su yi aure, ta mance gaba daya akwai Yan baya.... wani interpretation take son mutane suyi ma gidan nan, auren namiji ma ga abinda ya faru balle mace?? This is very serious...." Ammi dai ta kasa cewa komai sbda Mama Hadiza, Imaan ta taso ta dawo parlor don a rayuwarta na duniya bata son abinda xai 6ata ma Daddynta rai, Durkusawa tayi gefensa a hankali tace "Daddy ku yi hakuri" Daddy bai iya yace Komai ba.... Can Ya kalli agogon wrist dinsa yace "Ya Allah, just an hour remaining, Me xa mu ce ma mutanen nan fisabilillahi??" Ammi dai ba bakin magana, Mikewa Daddy yyi ya fita parlon, duk suka bi sa da kallo, Ammi ta sauke ajiyar xuciya, imaan ta mike a sanyaye ta wuce daki. Hijab dinta ta saka ta tafi part din Inna, suna xaune tare da ta Rasulu sun cika faranti da shinkafa jollof ga kaji kusan goma ana ta ci, turo baki tayi ta xauna tana kallon Inna a hankali tace "Inna don Allah ku yi hakuri ku bari ayi auren nan, kuna son a dinga ma su Abba kallon kananun mutane ne a garin nan?" Inna ta ajiye cinyar kazar dake hannunta tana kallonta baki bude tace "Shi Uban naki ne ya aiko ki in tafi in samesa yanxu?" Imaan tace "Ni ba wanda ya aiko ni" Inna na nuna mata kofa tace "Toh maxa kiyi ta kanki, tunda ba uwar ki aka xaga ba dama me xai dameki, gantalalliya ki ma je ki ji da lalurorin ki xa ki dinga tsoma baki a xancen manya kina yar yarinyar ki da ke...." A fusace Imaan ta mike ta fice a parlon, part dinsu ta koma ta shiga dakinta ta tadda Maryam a dakin, Maryam tace "Ina kika je?" Imaan ta xauna gefen gado tace "Wajen Inna mana, naje na mata magana ta xageni" Maryam tace "ke me ya kai ki, ni fa am happy gwara a fasa auren gaba daya... yarinyar da ta walakanta ni ranan farkon da muka hadu, I sooo hate her with passion" Imaan tace "Toh reputation din su Abba da Daddyna fa? Ae shine abun dubawan ba fasa auren ba" Maryam tace "It's just for sometimes dear, ke kina ga akwai wanda ya isa ya sa Inna ta canxa ra'ayin ta?" Shiru Imaan tayi, can a hankali tace "Na san me xan yi, I pray it works" Inna na bakin tap tana wanke kwanukan da suka ci abinci da ta Rasulu tana yan wakeken su shata na tale tale ta daga kai jin tafiya, Mikewa tsaye tayi tana washe baki tace "A'ahhhh sannu da xuwa Bukar, Sannu da xuwa...." Sadeeq dake sanye da tsadadden Gezna fari kal sai walkiya yake ya iso inda take yana murmushi yace "Sannu kaka, ke kam baki gajiya da aiki...." Inna ta xaro ido ta rike ha6a tace "Huuuu in gaji da aiki in mutu cikin wari Bukar, Allah ya tsareni... maxa shiga ciki gani nan tahowa na ma gama ae" Sadeeq ya cire takalmansa ya shiga parlon dake ta kamshin turaren wuta ya xauna saman lallausan rug din, Inna ta shigo tace "Bari in kawo maka abincin bikin da aka fasa, ai ko yayi dadi har da na fitina, yana nan ta Rasulu ta jido mana har da nama ba iyaka, ni dai hakorana har ciwo suka fara yi saboda cin kaji, yanxu ma ta Rasulun ta shiga wanka ne..." Yana murmushin sa mai kyau yace "Kaka ni a koshe nake wllh kuma lkcn Juma'ah ya kusa sauran yan mintuna..." Inna tace "Toh yi maxa ka tafi idan an sakko sai ka dawo" Yana shafa kansa yace "Ehh xan tafi yanxu kaka...." Tace "Toh ko in dauko maka darduma, jiya na wanke sa tasss nasa Maimoon ta goge min na feshe sa da turare" yar dariya yyi yace "A'a kaka Ina da darduma a mota, xauna mu yi magana" Inna ta dawo da sauri ta xauna tace "Toh gani Bukar, in ji lafiya dai???" Yayi sunkuyar da kai yace "Na ji abinda ya faru ne daxu...." Bai kai aya ba Inna ta fashe da kuka tana kunce ha6ar xaninta cikin rawar murya tace "Wllh abinda ya faru kenan Bukar shine yasa nace baxa a daura auren ba, ba ruwana, yanxu haka an fasa duk nasa a sallami bakin da suka xo" Sadeeq yyi kasa da murya a hankali yace "Don Allah kaka kiyi hakuri, kinga su Abba da Daddy baxa su ji dadin kallon da jama'ah xa su masu ba, gashi ana ganin mutuncin gidan nan, babba dama shi da hakuri aka san sa, kuma wanda aka cuta shi ake ba hakuri dama..." da sauri Inna tace "Inaaa Bukar ai tuni an fasa daurin auren...." Yace "A'a na fa ce kiyi hakuri kaka, kuma ni dai na san ki da hakuri... Ke babba ce fa Kaka" shiru Inna tayi tana matsar kwalla, can tace "Wllh ni dai kunyar ka nake ji Bukar" Yana murmushi yace "Toh don Allah ki janye batun fasa auren" Inna ta d'an yi shiru, can tace "Toh ai shikenan, sun ma kansu ni dai ba ruwana, kuma na hakura aje a daura auren" Murmushi sosai Sadeeq yayi yace "Yauwa Kaka Allah ya kara girma, na ji dadi sosai da kika dau shawarata, Allah ya kara girma" Inna tace "Toh ai dama meye amfanin babban da bai daukan shawara, hakuri kuma ai Allahn da ya halicce mu ma hakuri yake da mu balle ni, na hakura wllh, ga waya sai ka kira min Bukar uban Imaan dama ya fi saka abun a kai uwa kanwar uwarsa ce amaryar, oho dai kirasa ince masa su je su daura auren hankalin su ya kwanta" Yana murmushi ya amshi wayar yayi searching sunan da tace anyi mata Saving lambar daddy da shi ya kira sannan ya mika mata, Daddy na dauka tace "Toh ni dai ba ruwana Allah ma hakuri yake damu, ku je ku daura auren ni na hakura Allah ya saka min da alkhairi" bata jira cewar daddy ba ta katse wayar, Inna ta kalli Sadeeq tace "Ni Rukayyar ma bata taba min irin haka ba gaskiya, ban dai san shaidanin da ya makale a xuciyarta ba yau, amma dai gaskiya tatattce ne d'an iska, ya cuceta ba kadan ba yau, nace to ko radion da suka kunna ya cika gida ne yasa shaidanin ya samu nasarar rudar ta, amma gaskiya ni bata tanka ni kwata kwata a gidan nan, kuma har xaunawa take idan xata gaisheni, shi kuma Ahmadu sarkin xuciya har ya yanke hukuncin ta tafi gida, ni sai ta ban tausayi ma wllh...." Sadeeq dai sai kallonta yake yana murmushi yace "A dai yi hakuri kaka" tace "Atohh, biyayya iya biyayya dai suna min ni baxan masu sharri ba...." Daddy ne ya shigo parlon tare da Abba da kawu Bala, Inna na washe baki tace "Sannun ku da xuwa" Sadeeq ya gaishe su gaba daya da ladabi, Inna tace "Toh gaskiya duk babban da yace baxai dinga daukan shawaran yaro ba yayi asara, me yyi min xafi da xan bari inyi asara, wannan yaro Sadeeq dai ya shigo ya ban baki kuma wllh na hakura aje a daura auren Allah ya sa albarka, kamar daga sama ya fado min yanxun nan, wato har labarin ya baxu duniya Kai jama'ah.... Kuma da kun san ta yanda xa ku bi da ni da xancen bai yi tsayi ba haka ba duk baku da wayo, ni dai na yafe, aje a daura auren" Abba ya d'an yi murmushi yace "Toh madallah mun gode Inna, Allah ya kara girma, xa mu je masallaci ynxu lkci ya kusa" Inna tace "Toh ku tafi Allah maku albarka, Bukari kai ka dawo in xuba maka abinci don Allah har da kaji xuka xuka" Sadeeq na murmushi ya mike yace "Toh in sha Allah xan dawo" Bin bayan su Daddy yyi ya fita, Abba na kallon Sadeeq yace "Maa Sha Allah, I am very happy at ur contribution Allah ya saka" Sadeeq yyi murmushi bai ce komai ba, a haka suka fita gidan Abba na kiran wayar Mujaheed, Mujaheed was so shock da ya ji wai ai Inna ta hakura, kuma wai Sadeeq Bulasawa ne ya bata hakuri, har reaction dinsa ya ba Abbansa da Daddy mamaki, haka dai suka wuce mosque ana sakkowa masallaci kuma aka daura auren Mujaheed Ahmad da Safeenah Usman, ko jira Mujaheed bai yi su gaisa da abokansa da suka taho daga nisa ba ya koma gida, direct part din Inna ya nufa, Imaan na tahowa daga part din innar rike da warmer xata sha corner suka kusa cin karo da shi, fixgota yyi wanda hakan yasa ta saki abincin hannunta a tsorace, yana mata wani mugun kallo da idanuwansa da suka rine cikin tsawan da ya raxana ta yace "Uban wa ya aikeki ki sa saurayin ki yaje ya ma Inna magana? Uban wa ya sa ki????" *Imaan isn't for free* it's 300 via Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah Then u show ur evidence of payment via my WhatsApp number 07087865788Kasa cewa komai Imaan tayi tana kallonsa don ba karamin tsorata tayi ba, cikin tsawa yace "Ba tambayar ki nake ba sai na baki dirty slap?? Who sent you, waye ya aike ki??" Hawaye ya cika idonta ta sunkuyar da kanta bata dai ce komai ba, saketa yyi ya jingina da bango xuciyarsa na bugawa, ta tsallake abincin da ya xube ta wuce da sauri tana goge idonta ya bi ta da kallo har sannan kirjinsa bai daina bugawa ba, hade kai yyi da bango yana Kiran Allah a ransa, ya fi minti biyu a haka sannan ya juya da kyar ya nufi bangarensu yana jin idanuwansa na juya masa. Imaan na kwance daki da yamma idonta a lumshe duk da ba bacci take ba, wayarta dake kusa da ita ya fara vibrate, bude ido tayi tana kallon wayar, tun abinda Mujaheed yyi mata daxu take daki taki fitowa duk nacin da Maryam tayi da ita ta fito, gaba daya she is moody, a hankali ta dau wayar tayi picking ganin Sadeeq ne ke kiranta, sallama yayi mata daga daya barin, murya can kasa ta amsa, yace "Are you okay dear?" Shiru ta d'an yi sai kuma tace "Bana jin dadi" yace "Subhanallah baki jin dadi kuma, kin yi stressing kan ki da yawa kenan, what's wrong? I mean me kike ji ke damun ki?" Cikin sanyin bemurya tace "Ache all over" yace "Subhanallah, kin sha drugs din ki?" Ta gyada kai kamar yana ganinta yace "Ohk toh xan kawo maki wani yanxu sai ki sha shi da daddare, you will feel much better" tace "Toh" yace "Xan kira ki idan na iso" daga haka yyi mata sallama ta katse wayar ta ajiye ta rufe idonta. Biyar saura ya sake kiranta yana waje, Hijab ta saka har kasa, xata fito ta tuna birthday gift dinsa ta koma ta dauko flower din da cards ta saka cikin hijab ta fito, Few visitors ne a parlon nasu, ta tafi dakin Ammi ganin bata ciki ta fito, a balcony ta tadda Ammi da Mama Hansai, Ammi na kallonta tace "Ina xa ki?" Ta sunkuyar da kai tace "Ammi ba dadewa xan yi ba ana kirana a waje ne" Ammi na kallon hannunta dake cikin Hijab tace "Meye wannan kike boyewa a hijab?" Murmushi tayi kanta a kasa tace "Ammi ba komai bane, sako ne fa" Mama Hansai na dariya tace "Yi wucewar ki kinji" wucewa imaan tayi tana murmushi, Yana tsaye jikin motarsa idonsa sanye da glass ya sa kananun kaya, sunkuyar da kai tayi ta isa kusa da shi, da damuwa yace "Ya jikin" tana d'an murmushi tace "Da sauki" ya dauko wani leda a gaban motar ya mika mata yace "ki sha tablets daya each each kafin ki kwanta" Bata amsa ba ta fiddo hannunta dake cikin hijab ta mika masa flower din hannunta cikin sanyin murya tace "Happy birthday dear" still yyi yana kallon flower din ko kiftawa babu" lkci daya ya karba yana wara ido so happy yace "Waowww Thanks soo much baby I love it...." Ita dai murmushi kawai tayi, a hankali tace "i am happy u love it...." Ko bai fada ba she can see how happy he is, yana wara manyan idanuwansa yace "But baby how did you know I love flowers plss?" Ta langwabar da kai tace "I only guess" lumshe ido yyi murya can kasa yace "I feel like hugging you sweetheart" d'an murmushi kawai tayi ta dauke kai tace "Ni xan koma ciki, and I am sorry I won't be able to attend ur party saboda bana jin dadi" a sanyaye ta kare maganar, cike da damuwa yace "Ai na maki uxuri dear, Allah baki lafiya thanks a lot, I will give you a call later" a hankali tace "Ameen ngd" daga haka ta juya ta koma cikin gida ya bi ta da kallo still smiling. Mama Hadiza ce xaune parlon Inna tare da Ta Rasulu, cikin rashin jin dadi Mama Hadiza tace "Yanxu fisabilillahi kin kyauta min Inna, duk yanda na takarkare a kan an ci maki mutunci sai ki watsa min kasa a ido??" Inna tayi kasa da murya tace "Toh Hadiza shikenan ana ta bani hakuri ana hada ni da Allah sai in botsare kamar shaidaniya? Babba fa dama da hakuri aka san sa, baki ga yanda aka cika min parlon nan ba daxu ana bani hakuri har da su Audu d'an tsut, daga karshe sai kuma ga Bulasawa da kansa shi ma ya tako har parlon nan ya ce inyi hakuri, to idan dai ni ba tsohuwar banxa bace mai kunnen kashi mara jin magana Hadiza ai ya ci ace na yayyafa ma raina ruwan sanyi in hakura, kuma ni dai gaskiya Rukayya bata ta6a min irin haka ba, hau ne ya fada mata...." Ta Rasulu na nuna Inna ta kankance ido tace "Ke dai Asabe ki dinga jin tsoron Allah, nan kika maida mu mahaukata muna bambami daga karshe kika watsa mana kasa a ido wai kin hakura, Toh ai ina gida xa ki sa a kirani ki kawo min karar Rukayya, ba kuma ruwana wllh don baxan saurare ki ba, ke kuma Hadiza me xai dame ki?? Ai kadan da aikin Asabe kenan baki biyu, ni ban yi mamaki ba, ni ba dai ruwana ban ce komai ba in yi magana ta kullace ni, amma banda haka me aka yi aka yi wani shegen Bulasawa da har xai bata hakuri ta hakura? Bayan abinda tsinanniyar matar nan Rukayya ta mana, Kai Asabe Allah ya baki lafiya, ya kuma shirye ki, ni dai kin ga tafiyata nan...." Inna ta tsuke fuska tace "Toh ai ni ba gantalalliya bace da xa ayi ta ba ma hakuri in ki hakura kamar kafurar Bayan tsauni, ehe... Bulasawa kuma ni ya fi min kowaaa, yaro mai hankali da natsuwa mai magana irin ta manya, duk sai da ya fada min maganganu masu dadi da kwantar da xuciya wanda su Amadu suka kasa, toh ni ko me xance ma yaron Banda Allah ya masa albarka, ai in dai bai auri Imaan ba to sai dai in ni Asabe bana numfashi, Imaan ta sa ce in sha Allah, Bai fi min wasu 'yan uwan nawa ba ma ni Allah na tuba, Rukayya kuma ai tuni tana akurkin gidan da ta gina ma iyayenta sai kace ba ni ta ma rashin mutunci ba da xa a bar ta ta kwana gidan nan...." Ta Rasulu ta mike tace "Ni dai tunda kika kunya ta ni, kika kunyata Hadiza Allah sai ya saka mana ya bi mana hakkin mu, Rukayya kuma mu dai je xuwa muna nan dake xata dawo gidan nan...." Inna tace "Ke ni fa ban hakura da abinda Rukayya ta min balle ta dawo, ai Rukayya yar iska ce, aure ne dai nace aje a daura kada 'ya yana su ji kunya" Ta Rasulu tace "Oho dai ni kin ga tafiyata sai ki saka Bukar gaba ya bada kudin nan na laluran Imaan a san abun yi...." Daga haka ta fice daga parlon, Inna tace "Toh Allah bar xumunci ta Rasulu, Allah ji kan mai salati da jikan shehu, Allah ya saka da alkhairi ai ni kin gama min komai a duniya wllh kin fi min kowa ma, Allah ya bar mu tare sai kuma kin dawo bikin Imaan da Maimoon in sha Allah, Kai ae xan taho har gida maki ban gajiya, Bari dai 'yan kauyen nan su koma kauyukansu xa ki gan ni" Mikewa Mama Hadiza tayi ta fice daga parlon rai ba dadi, Inna ta bi ta da kallon gefen ido tace "Toh meye kuma axumi uku da xa ki yi, sai kace warce bata axumin Ramadan, Ni dai ba ruwana dama ban aike ki kiyi ta rantse rantse ba...." A ranan Mama Hadiza bata kwana gidan ba ta tafi gidan wata yayar Mai gidanta dake nan garin kadunan. Imaan na parlon Inna bayan isha tare da Maryam suna cin abinci aka bude kofa, kallon kofar suka yi Mujaheed ya shigo da sallama murya can kasa, wani daddadan kamshi ya gauraye parlon, yayi wani kyau na daban cikin milk shaddar jikinsa dake ta talli, Maryam na murmushi tace "Groom dama har yanxu baka tafi ba?" shi dai bai ce mata komai ba ya xauna, Imaan dai bata kalli inda yake ba tun bayan da suka hada ido shigowarsa, ta dinga cin abincinta a hankali, daga cikin dakin Inna tace "Mujaheed ne?" Maryam tace "Ehh" da sauri Inna ta fito ta marairaice tace "Tun daxu nake cigiyar ka Mujaheed, nace to ko har ka tafi wajen amaryar ne ba sallama ni patuu...." Kamar baxai ce komai ba sai kuma yace "Yanxu xan tafi" Xaunawa Inna tayi ta fashe da kuka a hankali tace "Shikenan yanxu Mujaheed sai dai ka xo ka gaishe mu ka tafi?? Shikenan ba kai ba kwana cikin gidan nan yanxu balle ka xo da sassafe ka gaisheni, wa xai dinga shigo min nan muna hira? Shikenan tafiya xaka yi ka bar ni yanxu, dama ba kowa gare ni ba sai Allah sai kai, kaine me debe min kewo gashi yanxu kayi aure xaka tafi gidanka ka barni ni kadai raina..." Mujaheed bai san lkcn da yyi murmushi ba sai dai bai ce komai ba yana danna wayarsa, Inna na share hawayenta cikin rawar murya tace "Rayuwa kenan, lallai sabo turken wawa, Allah ubangiji ya ba ku xaman lafiya da matar, in sha Allah xuwa nan da kwana biyu imaan xata rakoni don baxan gane gidan ba in xo ganin daki in sa albarka kuma in maku nasiha da amaryar, Allah ya sanya alkhairi... Ni dai baka taba min komai ba Allah maka albarka" Mujaheed na murmushi a hankali yace "Ameen" Mikewa yayi yace "Toh sai da safe" Inna ta kara rushewa da kuka har da rike kai, Maryam ta kasa ci gaba da danne dariyar da ke cinta, Imaan kam kin dago kanta tayi tana juya shinkafar gabanta, Cikin kuka sosai Inna tace "Shikenan kuma, wayyo rayuwa kenan...." Maryam na murmushi tace "Allah ya bada xaman lafiya Ya M.A, sai mun xo ganin dakin Aunty amarya" Mujaheed ya d'an yi murmushin karfin hali ya gyada mata kai ya juya ya nufi kofa, Inna na kallon Imaan da ta sunkuyar da kai tace "Toh ke baxa ki ma yayan naki fatan xaman lafiya da matarsa ba Imaan" Shi dai Mujaheed bai tsaya ba har ya fita, bin sa da kallo imaan tayi sai kuma ta mike ta bi bayansa da sauri, Maryam ta xaro ido tana kallon Inna tace "Wai kuka fa take yi..." Inna ta kara rushewa da kuka tace "Ka ji ki da wata magana, baxa ta yi kuka ba?? ke kinsan wahalan da Mujaheed yyi da ita tun tana tsumma, ke kinsan irin fadi tashin da yayi a kanta tana karama, to ko ubanta bai yi wahalar da Mujaheed yyi a kanta ba, kullum a makale da shi xa ki ganta duk ta takura bawan Allahn duk inda xa shi tana hannunsa, tayi ta basa wahala, har goyata ya sha yi, ta xo ta fara ciwace ciwacen da ba a san kansa ba nan ma babu irin wahalan da bai yi da ita na ganin ya nema mata lafiya ba, ai shakuwar dake tsakaninsu ko d'a da uwa sai haka, kuma kice baxata yi kuka ba yau xa su rabu na har abada" tana kai wa nan ta fashe da matsanancin kuka ta xamo daga kan kujera tayi xaman dirshan a kasa, Maryam dai sai dariya take kasa kasa. Imaan na fita parlon Inna taga har yayi nisa, ta bi bayansa da sauri tace "Yaya" tsayawa yayi ya juya yana kallonta, Bata san lokacin da ta fashe da kuka ba ta nufesa da gudu ta rungume sa cikin rawar murya tace "Xan yi missing din ka Yaya" kasa cewa komai yayi, lkci daya idonsa ya canxa launi, rungume ta yyi shi ma yyi ya lumshe ido, kuka ta dinga yi a kirjinsa, cike da karfin hali yace "Ae xa ki dinga xuwa gidana in sha Allah..." Ta gyada masa kai kawai hawaye na sauka idonta, cikin sanyin murya tace "Kayi hakuri da abinda nayi daxu, ban san it's wrong ba I wouldn't have done that, kayi hakuri plss...." A hankali yace "Na hakura" gently ya janyeta jikinsa ganin hawaye take har sannan yace "Toh ya isa haka mu je ki rakani gun mota" Bata iya ta ce komai ba ya kama hannunta suka nufi gate. Tafiya kawai suke kamar ba su son tafiyar har suka fita gate din gidan, suna isa motarsa ya juya yana kallonta har idanuwanta sun yi jajir, sunkuyar da kanta tayi a hankali tace "Sai da safe, I am wishing you a happy married life...." Yayi murmushin karfin hali yace "Thanks imaan" Juyawa tayi ta fara tafiya yace "Imaan" ta tsaya sannan ta juyo jin bai ce komai ba ta dawo inda yake tana kallonsa, yace "Shiga mu je xan siyo ma Inna abu ki kawo mata ynxu" a hankali tace "Toh" sannan ta xaga ta bude front seat ta shiga, ya shiga driver seat ya tada motar, the journey was silent har suka iso gun masu gashin kaji, yayi parking ya kashe motar, ya sauka, ba a dau lkci sosai ba ya dawo rike da leda uku na kaji da fresh milk, ya bude back seat ya ajiye leda guda sannan ya bude side dinta ya mika mata leda biyu ta amsa ya xaga ya shiga driver seat, gida ya koma bayan yyi parking ya juya yana kallonta yace "Sai da safe" ta sauke idonta kasa tace "Allah ya kai mu..." Yace "Ameen, ki dau daya sai ki kai ma Inna daya" D'an murmushi tayi ta bude motar ta fita, ta nufi gate ya bi ta da kallo har ta shiga sannan yayi reverse ya bar layin. Washegari asabar tun da wayewar gari Ammi da Aunty, Mama Hansai da matan kawu Bala suka dinga aiki a gidan trying to make sure everywhere was neat, masu kujeru dama su ma sun xo sun dau kayansu, su Maimoon, Ummi da Maryam kadai ke taya su aikin, Imaan kuwa na kwance dakinta wai kai na ciwo, Rahma dama tare da ita Umma ta bar gidan da yammacin jiya.... Bayan azahar Imaan na part din Inna tare da Maryam, Inna na kan darduma tana bada labarin nan dai na irin yanda aka haifi Mujaheed tana tsaye bakin kofar asibiti tun safe har dare, wahalan da tayi da shi tun yana tsumma, yanda ya girma a wajenta da fadan da yasa ta dinga yi da jama'ah a anguwa, har lkcn da ya tafi kasar waje karatu.... Imaan dai na kwance sai game take a wayarta tana tabe baki don ita dai har ta haddace labarin nan layi layi, Maryam sai dariya take ita da ba a ta6a ba ma labarin ba, Inna na matsar kwalla tace "Har xuwa jiya da aka daura masa aure, Allah sarki Mujaheed dina" Dariya kawai Maryam take har da kwanciya, Inna dai sai matsar kwalla take tace "Duk cikin 'ya yan Ahmadu babu ya shi, gashi duk ya fi su kyau wllh, ga tsafta ga mutunta na gaba da shi, sam Mujaheed bai san wani abu wai rashin kunya ba, bai taba mayar min da magana ba, wllh jiya ban yi baccin kirki ba da tunaninsa na kwana..." Sai kuma ta fashe da kuka sosai, sai a sannan Imaan tayi murmushi bata dai ce komai ba, cikin rawar murya Inna tace "Da dakunan bangaren nan nawa sun kai uku sai in ce su dawo nan da matar kawai ni dai in dinga ganin sa kullum" Maryam dai sai dariya take, Imaan ta mike ta wuce daki ta dalilin kiranta da ake a waya, Daga kiran tayi ta xauna gefen gado ta kai kunne hade da yin sallama, ya amsa yace "How are you dear?" Tace "Alhmdllh" yace "Hope kin ji sauki sosai" tana murmushi tace "Sure, sosai" yace "Ohk to ki dan fito ki amshi sako" ta xaro ido tace "Na me?" A hankali yace "C'mon dear" tana murmushi tace "Toh bari in fito" daga haka ta katse wayar ta fito parlor tana kallon Maryam tace "Mu je ki rakani" Inna na goge hawayen idonta tace "Ina??" Imaan ta turo baki tace "Ae yanxu xa mu dawo" Inna ta marairaice tace "Tou ni dai kar ku dade, mai tayani xaman gashi yayi aure ya tafi..." Dariya imaan tayi ta fita Maryam ta bi bayanta, har suka isa gate Maryam tambayarta inda xa su take yi amma ta ki gaya mata, suna fita gate din Maryam tayi shiru ganin Sadeeq tsaye kusa da motarsa, murmushi yayi ganinsu, Maryam tace "Hi...." Yace "Hello Maryam" tana murmushi tace "Happy Belated birthday Sadeeq" yace "Thanks much... Hope an gama biki lafiya?" Tace "alhmdllh" yace "Maa Sha Allah, Allah ya basu xaman lafiya" Maryam tace "Ameen" kallon Imaan da ta jingina da motar ta rungume hannu yayi a hankali yace "Hello princess..." Ta d'an yi murmushi tace "Ya gida" yace "Alhmdllh, ya Kaka?" Imaan ta langwabar da kai tace "tana ciki tana ta missing ya Mujaheed" Yace "Allah sarki, ta kwantar da hankalinta after a month sai ta koma gidan gaba daya koh" Yar dariya kawai imaan tayi tace "Gaskiya ne" yyi murmushi ya bude back seat ya fiddo da wani kwali dake a rufe amma ko bai fadi meye a ciki ba kowa ya sani, yana kallonta yace "Here..." Ta xaro ido tace "Haba wannan ai yayi yawa" yace "Ni ma sun min yawa, take plss baby" Imaan tayi murmushi ta d'an risina ta amsa tace "Toh Allah saka da alkhairi" hararanta yyi tayi dariya bata ce komai ba, wani box mai kyau ya fiddo ya mika mata ta make kafada tace "Bana so" hade rai yayi ya kalli Maryam dake murmushi yace "Kin ganta koh?" Maryam tayi dariya ta mika masa hannunta tace "Bani in rike mata" Mika ma Maryam box din yyi, Maryam tace "Allah ya saka da alkhairi" Yana murmushi yace "And ban mance promise da na maki ba, kin bar min xabi or you want anything?" Yar dariya Maryam tayi tace "Ehh na bar maka" yace "Toh shikenan, thank you" Kallon imaan yayi yace "Dear, we will talk later ki gaida kaka" Imaan tace "Toh xata ji nagode" Sallama yayi ma Maryam ma suka nufi gate, ya bude maxaunin driver ya shiga ya tada motar, suna shiga gida Maryam ta kashe ma imaan ido tace "Yau xa mu ci cake mu yi dam, amma me xa ki ce ma Ammi?" Imaan ta xaro ido tace "Part din Inna xan kai ai" Maryam tace "That will save u long explanation" Washegari Sunday tun da sassafe Inna ta gama shiryawa wai xa su gidan Mujaheed da Imaan, Daddy dake parlor xaune yana kallon news yace "Toh ai kila ma basu tashi ba da sassafe xa ki je masu Inna" Inna ta xaro ido tace "Sai kace rubabbu Bukar kace min basu tashi ba, Toh ni dai gaskiya na shirya kuma yanxu xan tafi ina imaan din?" Daddy yace "Bata tashi ba" Inna ta xauna saman kujera tayi tagumi tace "Naga abinda ya isheni.... baccin safe ko baccin asara ni Asabe, karfe takwas ace mutum mai rai bai tashi yyi wanka ya kintsa ya karya ya gyara gidansa ba? Kuma tun jiya nace mata ta shirya da safe xa mu tafi tare tunda wannan yarinya Maryam dangin ubanta sun xo sun tafi da ita jiya da magariba... Kai ku dai baku da tsari gaskiya... Meye kuma baccin safe??" Shi dai Daddy bai ce komai ba, Ammi ta fito daga kitchen ta gaida Inna sannan ta tafi dakin Imaan ta tasheta... Inna na ta xaune parlor ta tsuke fuska har imaan ta fito bayan kusan minti talatin cikin atamfa riga da skirt na biki da aka masu bata sa ba, sosai kayan suka amsheta, Inna tace "Ki dauko mayafi mu tafi idan munje can kya karya gaskiya...." Ammi da Daddy suka kalleta, can Ammi tace "A'a inna da dai ta karya ai bata da 6ata lkci wajen cin abinci, ta je gidan mutane da sassafe...." A fusace Inna tace "Ke dai Aisha ki daina haka, ki dinga jin tsoron Allah, Gidan Mujaheed din ne gidan mutane idan ba walakanci ba, gidan Mujaheed ne fa, ni dai ku dinga tsoron Allah sai kace wanda xata gidan 6are? Ke dauko hijabinki mu tafi, shi gidan yayan nata xaki ce ma gidan mutane saboda baki da mutunci..." Tana fadin haka ta nufi kofa a fusace, Daddy ya tabe baki bai dai ce komai ba, Imaan ta sa hijab ta dauko takalminta da wayarta tana kallon parent din nata a hankali tace "Sai mun dawo" Daddy kadai ne yace "Allah ya kiyaye" Ammi kam bata ce komai ba sai aikin gabanta take. *Imaan isn't for free* it's 300 via Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah Then u show ur evidence of payment via my WhatsApp number 07087865788Suna fitowa compound Inna ta kalli Imaan tace "Toh ko dai in je inyi ma Ahmadu magana ya sa direba ya kai mu?" Imaan dai bata ce komai ba, Inna tayi tsaki tace "Ayi ta maki magana kina ma mutane shiru idan ma baccin ne bai isheki ba idan munje gidan Mujaheed din ba sai a baki daki daya ki kwanta kiyi ta yi ba, ai can ma gida ne" Daga haka ta nufi part din Abba imaan na biye da ita, Aunty ce parlor tana goge goge da su Maimoon, Aunty ta xauna ta gaida Inna, su Maimoon ma suka gaisheta, Inna ta amsa tace "Gidan shiru ba wannan mata Rukayya koh" Ita dai Aunty bata ce komai ba, Inna tace "Toh Ahmadu nake nema ya kira wannan mutumi me jan mota ya kai mu gidan Mujaheed, tun asuba na gama shiryawa Imaan ta bata min lkci" Aunty tace "Toh xauna Inna ki jira driver din an aike sa yanxu" Inna ta xauna tace "So dai ake in makara kawai, Banda haka ni fa tun Asuba nayi wanka na" Imaan ta xauna a parlon bayan ta gaida Aunty tana kallon series din da akeyi, ba a dau lkci ba driver ya dawo, Aunty na kallon Inna dake xuba gyangyadi tace "Toh ya dawo fa inna..." Inna ta bude ido da sauri ta mike tace "Toh tashi mu je imaan, shi Ahmadun baya nan ne?" Aunty tace "Bacci yake" Inna tace "Ni dai ba wajena suka gaji baccin safe kamar rubabbu ba gaskiya" daga haka ta fita imaan na biye da ita, a waje suka tadda driver da mota, imaan ta bude ma Inna motar ta shiga tana amsa gaisuwar driver din sannan imaan ma ta shiga, sai da suka hau saman titi Inna na kallon Imaan tace "Toh kin gaya masa anguwar ne" Drivern na murmushi yace "Ae na san gidan kaka" Inna ta washe baki tace "Ashe har ku kunje kun sa ma gidan albarka ku ma" Shi dai bai ce komai ba yana murmushi, tafiyar kusan minti ashirin suka yi suka iso gidan Mujaheed, Inna na kallon driver da yayi parking a waje tace "Kai ya haka ka danna han a bude maka gate ka shiga mana, gidan jikana ne fa" Horn driver yyi mai gadi ya fito yana kallonsa, can ya karaso gun motar yace "Daga ina?" Rike baki Inna tayi da mamaki tana kallonsa tace "Naga abinda ya isheni, kai gidan jikana ne fa kake tambayar daga ina? Na shiga uku wai ni yake tambaya daga Ina, ko in sauko in bude get din da kai na ne" Mai gadin yyi kasa da kai yace "Yi hakuri Baaba" daga haka ya tafi da sauri ya bude gate din, Inna ta ja tsaki tace "Mutane dai ba tsoron Allah... wai daga Ina, ke ki ji fa gantalalle amma ba laifinsa bane na Mujaheed ne da bai sanar masa kakarsa na da rai ba" Ita dai Imaan bata ce komai ba driver ne ke bata hakuri, yana gama parking imaan ta bude motar ta fito, Inna na kallon driver din tace "Toh yi wucewar ka yaro, mu da gida kuma sai bayan isha in sha Allah" Yace "Toh baaba ku dawo lafiya" Inna ta nufi entrance din shiga gidan tana washe baki, Imaan dai na biye da ita, Bubbuga kofa Inna ta shiga yi da karfi tana cewa "Salama alaikum" Imaan tace "Kai inna kiyi a hankali mana..." Matsawa Inna tayi ta bude baki tana kallonta, Imaan ta turo baki ta danna bell tace "Kawai kiyi ta bubbuga ma mutane kofa da karfi" Inna xata yi magana aka bude kofar, Inna ta washe baki tana kallonsa tace "Mujaheed...." Kallonsu kawai yake yana tsaye bakin kofar sanye da jallabiya, Inna ta rike haba tace "Ashe da gaske ba ku tashi ba kenan" rabawa tayi ta gefensa kamar yar yarinya ta shige parlon, Imaan ta juya tana murmushi, can dai ta juyo a hankali, kallonta taga yana yi, ta sunkuyar da kai tace "Ina kwana Yaya" Muryar Inna suka ji a parlor tace "Ina amaryar??" Mujaheed ya juya ya koma parlon, Imaan ta bi bayansa, Xaunawa yyi yana kallon Inna yace "Ina kwana?" ta washe baki tace "Lafiya lau Mujaheed, tun asuba da na tashi nayi wanka wllh, Banda imaan da ta bata min lkci da tun gari bai gama wayewa ba xa ku gan ni" shafa kansa yyi bai dai ce komai ba, Inna na kallon pillow da aka ajiye kan lallausan sabon rug din parlon tace "Cewa nayi ina amaryar" Mujaheed yace "Tana sama...." Yana fadin haka ya tashi ya wuce sama, Inna ta kara kallon pillow dake parlor murya can kasa tace "Toh waye kuma ya kwana a parlor ni patuu" Imaan tayi murmushi tace "Toh ke ina ruwan ki" Inna tace "Atohhh, ba ruwana kuwa" Cire Hijab Inna tayi ta linke tana kallon parlon tana murmushi tace "Sabon gida ba dai sha'awa ba" Mikewa tayi ta nufi wani kofa ta bude tana lekan ciki ta karasa ta ajiye hijab din nata a ciki ta fito ta rufe tace "Dakinsu Hansai ne, shi ma sun xuba lafiyayyun kaya a ciki wllh masu tsada...." tabe baki tayi ta tafi ta bude kofar kitchen tana lekan ciki ta xaro ido tace "Waiii.... Ai kitchen din ma ba masaka tsinke da kayan kitchen na xamani, Ashe dai ba gwalagwalan karya aka dinga yawo da shi ranan casu ba" Imaan dai ta hade rai sai kallonta take... Mujaheed na haurawa sama ya bude dakin da Safeenah ke ciki, bacci ya sameta tana yi, ya shiga ya kulle kofar ya karasa kan gadon ya d'an bugi gadon yana kallonta, sai da ya buga gadon da karfi for d second time sannan ta bude ido ta mike xaune tana kallonsa da wani expression, yace "Kin ma yi sllhn kuwa?" D'an tsaki tayi tace "Haba don Allah sai ka wani buga gado ka tsorata ni kamar xaka tada kato??" Daga head har toes yake kallonta, ta tabe baki ta kalli agogo tace "Sllh dai dole inyi ko karfe nawa ne" da mamaki yake kallonta yace "A gidan ku haka kike kai wa har karfe tara baki yi sllh ba Safeenah?" A fusace tace "Toh gajiyan bikin fa? Plss Mujaheed that's not how to treat a new bride you are not romantic, haba don Allah sai kace mun ta6a rayuwa gida daya...." Wani kallo kawai Mujaheed yake mata, strictly yace "Look Safeenah I won't tolerate this, gidana ba na kafurai bane, tun asuba na shigo na tashe ki kiyi sllh shine har yanxu baki yi ba, is this ur home training?" Yar dariya tayi tana kallonsa daga sama har kasa tace "Kai ko kunya baka ji ba don Allah??" tana kwaikwayonsa tace "Wai wani tun asuba na shigo na tashe ki.. ban taba jin labarin ango irin ka ba sai yau da nake gani a xahiri a gidana, wai ka shigo min da asuba, ain't you ashame of ur self plss" murguda baki tayi ta sauka daga saman gadon da yar figigiyar rigar baccinta ta nufi bathroom, ya bi da kallo kafin ta shiga bayin yace "Ki sameni downstairs yanxu idan kin yi sllhn" daga haka ya juya ya fice daga dakin, Tv ya tarar Inna na kokarin kunnawa tana cewa "Toh sai me idan Baki kunna min ba kamar yau na saba hada kayan kallo kuma... Gidan Mujaheed kuma baxa ki saki jiki kiyi yanda kike so, ban da shi wa gare ki da xa ki je gidansa ki sake jiki dama, ni dai ba ruwana, ki dinga abu domin Allah Banda munafurci" Imaan dai sai kallonta take fuska daure, Inna na ganin Mujaheed ta mike tace "Wai ka ji daga nace ta hada min kayan kallo shine xata ce min daga xuwa gidan mutane, su waye kuma mutane, Mujaheed din koko Amaryar da bata fito gaisheni ba har yanxu, ni dai ba ruwana, idan ma xa ki cire Hijabin nan na jikinki ki linke ki ajiye ki tsayar da ranki waje daya ki saki jiki kamar kina gidan Bukar to gwara ki cire don da kyar ma ba kwana xamu yi a nan ba gaskiya, ga dai dakuna na kirga har hudu ranan" Mujaheed ya karasa ya kunna mata tv din yace "Xata sakko yanxu ta gaishe ki ai" Inna ta koma kan kujera ta xauna ta tsuke fuska tana kallon Tv, Xaunawa Mujaheed yayi kan kujera ya kalli Imaan ta gefen ido, Sai turo baki take, Mujaheed ya kalli Inna yace "Amma kuma sai ki yi irin wannan sammako Inna" Inna ta kallesa da sauri tace "Ni dai Ahmadu ne yace in taho da sassafe, bayan jiya ya shigo da daddare mun yi magana" Imaan ta xaro ido tana kallon Inna, Murmushi Mujaheed yyi yana gyada kai, Jin taku a stairs ya juya, Safeenah ce ke sakkowa sanye da doguwar riga damamme, Still tayi tana kallonsu, Inna ta kankance ido tana kallonta da kyau ita ma, Safeenah ta hade rai ta karasa sakkowa ta shigo cikin parlon, Mujaheed ya kalleta yace "Meet my grandma and my lil sis Imaan...." Inna na washe baki tace "Sannu Amarya, da fatan dai an tashi lafiya" dauke kai Safeenah tayi ta tabe baki murya can ciki tace "Ina kwana" Inna tace "Lafiya lau, sai dai ko sunanki ban sani ba" Mujaheed yace "Safeenah" Inna tace "Toh madalla, to safeenah Mujaheed dai gashi nan a gabana aka haifesa, kuma ni nayi wahala da shi tun yana tsummarsa, ke wahalar da nayi da shi wllh kare baxai ci ba, Tabb banda nakudarsa me Rukayya tayi???" Hade rai Mujaheed yyi yana kallonta, Safeenah tace "Toh maa sha Allah, ina d'an yi abu ne a sama Hajiya...." Xaro ido Inna tayi kafin tace komai Mujaheed yace "Mind you, Inna is what we call her..." Safeenah ta d'an tabe baki tace "Toh xan je in yi abinda ke gabana a sama Inna" Inna tace "Ba xancen kije kiyi abinda ke gaban ki ba Yar nan, ko karyawa fa ba mu yi ba, Imaan ma ina jin ko wanka bata yi ba don da naje ma bacci na tarar tana yi...." Imaan na kallon Inna tace "Ni bance maki ban yi wanka ba inna" wani matsiyacin kallon Safeenah ta jefa mata sannan ta kalli inna bluntly tace "Ba a kai ga sauke min gara na daga container da ya kawo ba, ba komai yanxu haka s gidan" Wani kallo Mujaheed ya dinga mata trying hard to control his temper, inna ta rike ha6a tana kallonsa tace "toh me ku ke ci a gidan ba a sauke gara ba ni 'ya su?" Safeenah tayi wucewarta sama, Mikewa Mujaheed yyi ya bi bayanta, yana shiga dakin ya kulle kofar yana nunata da yatsa cikin tsawa yace "Let me give you this warning Safeenah, idan baki son na fito maki da the other side of me you've got to respect that woman to the fullest, she is my grandma kuma albarkacin ta yasa kike gidana, wllh wllh xan yi taking action din da xai baki mugun mamaki idan baki maida hankalin ki ba, sannan breakfast ni nace ki tashi ki fita kije ki girka masu yanxun nan...." A tsawace ya kare maganan yana kallonta, Gaba daya ta gama tsorata sai kallonsa take tana komawa baya, lkci daya hawaye ya kawo idonta sai kuma ta fashe da kuka tace "Is this the real you dama Mujaheed?? me yasa tun farko baka yi encourage dina wajen ganin nayi kokarin hakura da kai ba, you are always telling me xaka koyi sona I shouldn't worry, dama ka aureni ne to make life a living hell for me, kasan irin mutanen da na ki amincewa da nace sai kai?? Kasan mutanen da na watsa ma kasa a ido nace sai kai, dama laifine son mutum da xuciya daya?? Tun da aka kawo ni gidan nan ka ki ko da xama na minti ashirin a dakina balle ka kwana, wllh ina sonka Mujaheed, ban aure ka saboda komai ba sai saboda Ina son kasancewa da kai, ka dai san irin gidan da na fito balle kace saboda wani abu naka na aure ka" dauke kai Mujaheed yyi xuciyarsa na bugawa, right from time a rayuwar sa na duniya ya tsani ganin hawayen mace, a hankali ya karasa inda take ya xauna gefen gadon ya jawota jikinsa cikin sanyin murya yace "I won't make my home a living hell for you Safeenah, and sure I will create a soft spot for you soon, but you've got to respect my family, duk abinda nace bana so kuma plss try to avoid that, Kinga ke yan uwanki baxa su xo in masu gaisuwar walakancin da kika ma grandma dita ba...." lamo tayi jikinsa tace "Amma kana ganin wannan yarinyar fa bata gaisheni ba ma" Shiru ya d'an yi, Sai kuma yace "Mind you sunanta Imaan, and kar ki damu xan mata magana" tace "Step sis dinka ce?" Ya girgixa kai a hankali yace "She is my cousin sis" daga kai tayi tana kallonsa, ya gyada mata kai, tabe baki tayi bata ce komai ba, yace "Toh for my sake kiyi hakuri ki hada breakfast din even if it's just Irish and egg, sai ki dafa ruwan shayi" Shiru tayi masa yace "Xa ki yi?" A hankali tace "Toh" murmushi yyi ya manna mata kiss a goshinta, ta lumshe ido don ba kadan ba taji dadin hakan, ya mike yace "Come out soon" daga haka ya nufi kofa ta bi sa da kallo, Allah yasan so ba na wasa ba take ma Mujaheed, Bata taba yi ma d'a namiji irin son da take masa ba, kuma xata iya yin komai a kansa. Mujaheed na dawowa parlor ya tadda Imaan kadai tana kallo, tun da ta kallesa sau daya ta dauke kai, ya isa kusa da ita yace "Me yasa baki gaida Safeenah ba?" Ta turo baki ta ki cewa komai, ya dafa kujeran da take xaune yana kallonta da kyau yace "Look, duk kika xo gidan nan ko kika ganta a wani waje dolenki ki gaidata coz she is my wife... Kin ji abinda nace??" Ta hade rai tace "Toh ai ita ma ba da respect ta gaida Inna ba da ta sakko, so why will I greet her, why??? beside she is suppose to tell me... Sannu da xuwa kafin in gaisheta, amma ko kallona bata yi ba so nima naki gaisheta din ai ba wajenta muka xo ba...." Kallonta kawai yake ganin yanda take maganar cike da tsiwa tana xare masa ido, ya dauke kai ya d'an yi murmushi, can dai ya mike ya nufi kitchen jin muryar Inna kasa kasa ita kadai tana magana, tsaye yyi bakin kofa yana kallonta tana duke tana fere dankali tana cewa "Idan ba jaraba ba da safen ma ya wani bi figaggiyar mata kamar xabiya daki bayan kwana da yayi a dakin daren jiya, to meye xasu shige daki kuma da safe bayan nace masu ban karya ba ga 'yar mutane na taho da ita, ita ma bata karya ba, dama da ya iyayenta suka yarda ta biyoni, ni dai ba ruwana..." Dariya sosai ta basa, tana ganinsa tayi shiru tace "A'a har ka fito Mujaheed" yace "Dankali kike ferewa da kanki kuma?" Inna tace "Yo baxan fere ba tunda na kwaso yunwar cikina Mujaheed, ga Imaan ma bata karya ba da kyar Bukar ya yarda ta biyo ni... Abu dai da raina da lafiya ta, ita wancan matar dake xaune parlor tace ba ruwanta baxata shiga kitchen din mutane ba, ni ban gane ma wannan abun ba gaskiya" ya shafa kansa yace "Yanxu Safeenah xata xo ta hada maku kayan karin" inna ta ajiye wukar tace "Toh amma anya ka ce mata nice na raine ka kuwa...." Safeenah na sakkowa parlor ta dinga yi ma Imaan wani kallo sak na tsana tana tafiya, suna hada ido Imaan ta tabe baki ta dauke kai.... Tsayawa Safeenah tayi tana kallonta xuciyarta na tafarfasa tace "Beware a gidana kike.... you had better respect ur self ki maida hankalin ki" Kallonta Imaan tayi da sauri tace "Gidan ki ko gidan yayana? Gidan ku na can kin baro sa malama don haka baki isa ki min warning a gidan Yaya ba...." Da sauri Inna ta karasa fitowa kitchen jin muryar imaan, Mujaheed ma ya fito ya tsaya kallonsu da mamaki, Inna tace "Lafiya?? me ya faru??" Imaan tace "Wai inna ki ji ce min take in shiga hankalina wai nan gidanta ne, wllh ba abinda na mata daga sakkowarta ta fara min fada tana min warning" sake baki Inna tayi tana kallon Safeenah tace "Ba lafiya, ta shiga hankalinta kuma? Kinsan wacece ita kuwa yar nan, to bari kiji wllh wannan da kike gani ta fiye ma Mujaheed ke so dubu dari, kaji min mata kamar zabiya dai, ita da gidan yayanta kice ta shiga hankalinta sabida baki da tsoron Allah?? To wllh a kan Imaan sai Mujaheed ya kora ki gidanku yanxun nan, gwara ma ki xageni da ki ta6a min imaan gaskiya, duk da dai kin ma xageni tun daxu kawai dai ni me hakuri ce na ja bakina nayi shiru, kaji min mokadaddiyar mata dai xata sa min jika a baki in shiga uku???" Mikewa Imaan tayi kamar xata yi kuka ta nufi kofa tace "Ni sai kin dawo Inna baxan xauna ba...." Inna ta saki salati tana tafe hannu tace "Na shiga uku ni patuu, Mujaheed ya auri jaraba tunda ta ta6a imaan, ke me ya kai ki kinsan wacece kuwa, ita kenan fa uban ya haifa a duniya, ko kallon banxa ba a mata balle a mata fada... Shi Mujaheed din bai xaunar da ke ya sanar maki bane??" Bin bayan Imaan Mujaheed yyi ganin har ta fice parlon. *Imaan isn't for free* it's 300 via Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah Then u show ur evidence of payment via my WhatsApp number 07087865788Har Imaan ta sauka Balcony ta nufi gate Mujaheed ya rikota da sauri yace "Kee ina xa ki??" Ta hade rai kamar xata yi kuka tace "Ni dai gida xan wuce bayan ta gama xagina, Ni wucewa xan yi" Kallon Eyeballs dinta kawai yake, xata kwace hannunta ya kalli gate, lkci daya ya jawo ta kusa da shi murya can kasa yace "Toh kiyi hakuri...." ta turo baki ta ki cewa komai, ya dauke kai yayi murmushi yace "Toh baxa ki hakura ba..." Bata fuska tayi tace "Xagina fa tayi..." ya xaro manyan idonsa still smiling ya ja dogon hancinta yace "Ni ban ji inda ta xage ki ba, har da sharri...." Kwace kanta take son yi xata wuce ya ki saketa yace "Ai fa nace kiyi hakuri koh?" Kallonsa tayi fuska daure kamar xata yi kuka tace "Toh baka gaya mata ni wacece bane?" Dariya sosai ta basa, and he couldn't help it don har sai da yyi dariyan ganin maganan sak yanda inna ke yi, ya kamo duk hannunta biyu yace "Haba na gaya mata mana lil sis, amma kiyi hakuri xan sake gaya mata da kyau, yanxu mu koma ciki sai ki hada maku breakfast din mu rabu da ita...." imaan ta turo baki bata dai ce komai ba, yana murmushi yace "Idan mun koma sai kice ma Inna kin hakura don ta daina fada kin ji pls?" A hankali tace "Na ji" Yana kallonta sosai yace "Good girl" daga haka suka koma parlon yana rike da hannunta, Inna kadai ce tsaye parlon tana kallon stairs tana cewa "Ka ji min jarabbiyar mata ta ja Bukar ya kullace ni tunda ni na fito masa da 'ya har xa a sa ta a baki... to wllh hir dinki ni ba ruwana, to Wai ma ke baki da tsoron Allah ne?? duk hakurina yau sai da kika kai ni bango, banda haka kin fito daxu kin gaida ni a tsaye sandandan kamar katon soja, ni dai ban kula ki ba don babba da hakuri da kauda kai aka san sa, sannan na maki magana bamu karya ba kince kwantenar karyar da aka maki na gara bai sauka ba, ko ina aka taba gara a kwantena??? Ni dai duk ban kula ki ba ina ta hakuri shine yanxu xaki ta6a imaan baki san ba a ta6a min ita ba, to haka xa mu yi dake tun ban dawo gidan gaba daya ba?? Yau naga abinda ya isheni... Irin xaman da xa mu yi kenan ni patuuu da wannan figaggiyar yarinyar" Mujaheed ya karasa gun Inna yace "Haba Inna daga xuwa kuma, Imaan din fa ta ma ce ta hakura..." Inna ta kalli Imaan da sauri tace "Wai??" Imaan ta gyada kai a hankali, Inna ta koma ta xauna tana share xufar goshinta tace "Toh Alhmdllh... Sai ta sakko ta hada mana karin kumallo, gaskiya Mujaheed Ina ga baka yi dacen mata ba, tun fa ba aje ko Ina ba ta fara nuna hali, ko da yake ai ni me iya saita mata xama ne, ba haka na saita Rukayya ba ma Allah na tuba" Mujaheed ya kalli Imaan ya mata alamar da ta tafi kitchen din, ta rungume hannunta tace "Toh ni kadai?" Kallonta Inna tayi da sauri tace "Ke kadai me?" Mujaheed ya nufeta yace "Toh mu je" Ba musu ta nufi kitchen din ya bi bayanta, dukawa tayi gun dankalin da Inna ta fara ferewa, ya dau wukar ya mika mata yace "Be careful with the knife...." Bata ce komai ba ta amsa ta fara fere dankalin, ya duka kusa da ita yana kallonta, duk wanda ta gama ferewa sai ta sa a ruwan da ke kusa da shi, shi dai kallonta kawai yake, pieces shidda ta gama ferewa tace "Ai dai wannan ya ishemu ni da Inna..." Ya wara ido yace "Toh ni fa...." Kallonsa tayi da sauri tace "Har da kai?" A hankali ya gyada mata kai, ta tabe baki ta ci gaba da ferewa, wani kara tayi ta jefar da wukar sai ga jini a hannunta, ya daga ta da sauri yace "Subhanallah..." yarfe hannun ta fara yi a rikice tace "Wayyoo Yaya zafi...." Pampo dake kitchen din ya nufa da ita ya kunna yana tsaye bayanta ya shiga wanke mata hannun yana kallon cut din that isn't deep, a hankali yace "Sorry lil sis...." Yana gama wanke mata ya juyo da ita, hawaye ya gani idonta, lkci daya ya rikice yace "Yana maki xafi sosai ne??" ta fashe da kuka a hankali tace "Ba kai bane kace in kara bayan na gama namu da Inna" rungume ta yayi yace "Toh yi hakuri plss, we should have use the potatoe peeler instead" ya daga kanta yana share mata hawayenta da fingers dinsa, turo baki tayi tace "Ni dai sai dai kayi slicing din dankalin baxan yi ba" murmushi yayi yana ci gaba da goge mata idonta a hankali yace "Toh naji, sai ki kunna gas ki debi mangyada a pan" daga haka ya saketa ya koma gun dankalin, fry pan da ta gani ta dauko ta bude jarkan sabon man gyada ta deba a fry pan din sannan ta kunna gas ta daura, ta daura ruwan shayi ta sa lipton, ba dai kayan kamshi tunda bata san inda suke ba, tsaye tayi bayansa tana kallonsa har ya gama slicing dankalin ya mike ya ajiye bowl din a sink, ya juya yana kallonta yace "Toh ya xa ayi?" Yar dariya tayi tace "Baka sani ba Yaya" ya buda hannu alamar bai sani ba din, ta karasa inda yake ta wanke dankalin ta tsane duk yana kallonta, yace "Ke da ba ki girki a gida ma...." Murmushi tayi tace "Ehh amma ai ina ganin Ammi na yi, kuma dai na iya...." Shi dai bai ce mata komai ba, suna tsaye kitchen din har dankalin da ta xuba a mai ya soyu ta kwashe a plate, tana kallonsa tace "Toh ina eggs din?" Ya xaro ido yyi yace "Are you sure, kar kije ki tada min Asthma..." Ta turo baki tace "It's just an ordinary egg, sai in sa onion fa, ba yaji ai" Yana murmushi a hankali yace "Ohk...." Eggs din ya fiddo cikin few minutes ta fara soyawa bayan ta yi chopping onion a board, duk yana lura da ita to make sure she is fine din da gaske, can ya karasa kusa da ita ya tsaya bayanta a hankali yace "You are uncomfortable Imaan" ita dai bata ce komai ba don da gaske tsarkewa numfashinta yake yi ko don bata yi lowering gas din bane amma a gida ai tana soya kwai, ya rage gas din sosai ya juyo da ita tana facing dinsa giving her support with his broad shoulder, a hankali take sauke numfashin hade da shakar kamshin sa mai dadi, ya dinga juya kwan a frying pan har ya ga ya soyu sannan ya kashe gas din, gaba daya ya juye a plate din da ta dauko, ya kashe gas da ta daura ruwan xafi ganin yana tafasa, daga kanta yyi yana kallonta a hankali yace "Are you okay?" Kai ta gyada masa, yace "Ki tafi parlor xan kawo breakfast din yanxu" Bata ce komai ba ta nufi kofa ya bi ta da kallo har ta fita, wani plate din ya dauka ya debar ma Safeenah dankali da kwan ya rufe, sannan ya juye ruwan xafin a flask ya dauka da cups biyu da spoon ya tafi parlon, Inna na xaune sai shar6an bacci take har da minshari, ya d'an yi murmushi yana kallon Imaan dake xaune kasan rug ya ajiye flask din hannunsa yace "Are you sure you are okay?" Ta gyada masa kai, kitchen ya koma ya dauko plate din dankalin ya ajiye masu ya koma kitchen din, Tea mai kauri ya hada a cup sannan ya fita da kayan shayin ya ajiye, plate din dankalin da ya bari a kitchen din da cup din shayi ya tafi ya dauka ya fito, sama ya nufa imaan ta bi sa da kallo, can ta tabe baki ta dauke kai, Safeenah na dakinta tana waya da Mahaifiyarta ta sanar mata duk abinda ake ciki tun shigowar Inna gidan da sassafe, rai bace Hajiyan Marafa tace "Ban da ma kin nace sai shi Allah na tuba me xa ki yi da d'an wajen Rukayya, Ni fa da Rukayya kar ta san kar ne shi sa ban so auren ba, ke kuma kika ce ba ki san xance ba kin samu miji, amma duk wannan mai sauki ne wllh tllh, ni nasan ta yanda xan billo ma lamarin, ki kwantar da hankalin ki sai kace ba ni na haife ki ba dai, ai in sha Allahu yanda nake xaune hankali kwance ba damuwar kowa gidan ubanki haka ke ma xaki xauna gidan Mujaheed Safeenah in sha Allah" Safeenah na goge idonta tace "Toh Mummy..." Hajiyan Marafa tace "Kar ki nuna masu komai, har ita yarinyar me maki rashin kunya kar ki tanka ta, dama tunda Hajiya Rukayya tace min bata san wannan tsohuwar ba a wajen dinner nasan karya kawai take, amma ba damuwa... Ki kwantar da hankalinki dota babu mai sa maki ciwon kai in sha Allah a gidan auren ki, xuwa gidan ki ma sai ya gagare duk danginsa har ita munafukar uwartasa in dai ina numfashi, sannan kin ce har yau bai kwana dakin ki ba ko???" Daga kai Safeenah tayi jin an bude kofa da sauri tace "Mummy xa mu yi waya anjima" Bata jira cewar Mahaifiyar tata ba ta katse wayar, hade rai tayi ta kwanta ta juya baya, Mujaheed ya ajiye abincin hannunsa ya xauna gefen gadon yace "Plss plss kiyi hakuri Safeenah, nasan this is not proper at all cause this is just ur 2nd day a gidana, but plss keep this in mind haka grandma dina take wllh, kowa ya santa kece dai da baki santa ba, har ni ba barina tayi ba sai dai idan ban yi abinda xata yi magana ba, Imaan kuma bata da matsala kawai ba ku fahimci juna bane, she's very nice and sweet to stay with, ko a gida Grandma bata son a ta6a ta be it me or anybody... Ranan xa a ga the other side of her in har aka ta6a imaan kinsan takwararta ce, so plss you need not to worry beside just few hours fa xa su yi su wuce, and I assure you baxan yarda a taka ki ko a raina ki ba coz you are my wife...." Ita dai Safeenah bata juyo ba balle ta tanka sa.... Yace "Ga breakfast din ki" still taki cewa komai, Juyawa yayi ya koma downstairs, kallon Imaan da ta wani hade rai ya dinga yi har ya shigo parlon yace "Baxa ki hada shayin ba...." Kamar jira take tace "Ni ba yunwa nake ji ba dama ai" *For the sake of My lovely Naomi Baba Abbasss ga nyt update after enough read mores daxu da safe, duk da dai ba wani kirki gareta ba oo* 😍 _You are reading imaan for free and still telling me nonsense and posting in groups ur *Big Wahala*_🤷🏻‍♀️ All I know Is that my book Imaan isn't for free. Gbamm!! *Imaan isn't for free* it's 300 via Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah Then u show ur evidence of payment via my WhatsApp number 07087865788Shiru Mujaheed yyi yana kallonta, can ya karasa kusa da ita yace "Saboda me baxa ki ci ba?" Kin cewa komai tayi, yyi murmushi ya xauna kusa da ita ya jawo cup da flask ya fara hada shayin, yana gamawa ya ajiye cup din shayin gabanta da plate din dankali, dauke kai tayi xata mike ya rikota, ta shiga kokarin kwace kanta tana cewa "Nace maka ni ba yunwa...." muryar Inna suka ji tace "Lafiya?? meye haka??" Saketa Mujaheed yyi da sauri, Inna na xaro ido tace "Lafiya kake matse yar mutane Mujaheed?" Ta gefen ido ya kalleta bai dai ce komai ba, Inna ta kalli Imaan tace "Me kika masa?" Kamar xata yi kuka tace "Inna nace masa na koshi fa shine wai sai na ci" Inna ta bude ido sosai tace "A'a toh ke kuma baki da tsoron Allah, kika koshi a Ina? Uban me kika ci? Bata fa karya ba Mujaheed... Ni dai ba ruwana, ka rabu da ita ka kada min nawa shayin in sha, ya wuce Allah ya masu hisabi da hanjin cikin nata" Murmushi kawai Mujaheed yake ya gama hada ma Inna shayin ya ajiye gabanta ya debar mata dankalin ta sakko kasa tace "Toh burodi fa?" Yace "Bari in fita in siyo yanxu" Inna tace "Atoh, na taba ganin inda aka sha shayi ba burodi dama" mikewa yayi ya fita parlon Inna ta bi sa da kallo ta rike ha6a tace "Ikon Allah, aure mai saita mutum ya gyara sa, dubi fa wani biyayya na musamman da Mujaheed yake yi yanxu daga ya kwana daki daya da mace, Ikon Allah ya fi gaban haka.... Mujaheed ne xan aika da ya tafi babu musu?? Lallai kamar Rukayya ta tsine masa, ai baxai ma je bane sai ya gama ja min rai ya gama min walakanci, ke ma dai Bulasawa yayi yayi ya yunkuro ayi auren nan ko kya yi hankalin, kinsan fa da ace ke ce kika yi aure da har na gama tarewa can gidan naki, toh wai yaushe ne wannan kaddararren jarabawan sakandarin ne ni patuu, wllh su Ahmadu da Bukar dama can basa tsoron Allah tun tasowarsu kamar dai ba ni na haifesu, Banda haka wani shegen jarabawa ne ya isa ya hana sunnar manzon Allah S.A.W.... Ni dai ba ruwana" Imaan dai bata tanka Inna ba sai fiffita shayin da Mujaheed ya hada mata take ta sha da sauri kafin ya dawo, Inna ta saki baki tana kallonta da sauri tace "Ya haka xa ki handame dankalin gaba daya Imaan, ba namu bane mu biyu" sosai ta ba Imaan da ta cika baki da dankali da kwai dariya, ko sauraranta bata yi ba ta dinga turawa har sai da ta ci kusan rabin plate din da kwai, Inna dai sai kallonta take baki bude, Imaan ta dau wani cup ta dinga fiffita shayin har ya huce ta kwankwade da sauri ta ajiye kusa da Inna tana goge bakinta, Inna ta rufe bakin da ta sake tace "Kunyar Mujaheed din kike yanxu ko me?" Da sauri Imaan tace "Kunya Kuma??? Ni dai kar ma ki ce masa na ci komai a nan, don ba abinda na ci" Bata jira cewar Inna ba ta koma kujera ta xauna tana goge bakinta da kyau, Inna tace "Dama mana, ya xa ayi ki iya cin rabin plate din dankali kamar jaka ai sai dai ni din..." Imaan dai bata kulata ba ta mayar da hankalinta kan Tv, Da sallama Mujaheed ya shigo parlon rike da ledan bread l, ya karaso ciki yana kallon empty cup din shayin da ya hada kafin ya fita, Imaan ta wani daure fuska tana kallon TV, Inna tace "Toh ba kya daure fuska ba dama kin handame komai kamar mayunwaciya, wllh Mujaheed yanda ka san ta shekara bata ci abinci ba, dubi abinda ta bar min fisabilillahi, ko mage aka bar ma wannan xata koshi balle mutum irina, yarinya dai sai ci kamar saniya" Imaan sai kallon Inna take kamar xata yi kuka, Mujaheed dai yayi murmushi ya ajiye bread din hannunsa yace "Toh tunda dai ba da kudin ki aka siyo kayan abincin ba kuma ba Amadun ki ko Bukar suka siyo ba me xai dameki? Gidan yayanta ne fa" Bai jira cewarta ba ya wuce sama, imaan ta dinga kallonta tana murmushi ranta fess, tabe baki Inna tayi ta bude bread din ta yagi kato a ciki a hankali tace "Toh da ban haifesu ba xa su haife ku?? da na sani ma in ki haifan nasu in ga ta tsiya, sai in ga ta yanda xa a same ku gantalallu kawai marasu tarbiya" sakkowa kasa imaan tayi ta dinga 6a66aka dariya, ita dai Inna bata ko kalleta ba ta tsuke fuska tana cin bread. Sai da tayi nakk dama ta mike ta kai plate da cup kitchen duk ta wanke duk abinda aka bata ta kife ruwan ya tsane sannan aka fara goge gogen kitchen din har wall din kitchen dai sai da ta goge sannan ta fito ta share parlorn tasss, sannan aka fara goge goge, tana goge sabbin kujerun da d'an kyallen da take goge goge tace "Babu wanda xai ce datti baxai fito daga parlon nan ba, kaii aji tsoron datti, datti ba kyau...." Ita dai Imaan kallonta kawai take, Inna ta gama goge goge ta wuce dakin su Hansai ta kwanta saman gado, nan ta dinga sharar bacci uwa tana dakinta. Sha daya da kusan rabi Mujaheed ya sakko parlon sanye da kananun kaya da suka amshe sa sosai, ya dinga kallon Imaan yana tsaye kusa da stairs, can yace "Ina Innar" ba tare da ta kallesa ba tace "Nima ban sani ba" juyawa yyi yana kallon Safeenah dake sakkowa a bayansa kamar mai tausayin stairs din, riga da skirt ne jikinta na atamfa da suka amsheta matuka, kayan ya haska ta ba kadan ba, she's really beauty.... fuskarta babu walwala har ta karasa sakkowa, tunda suka hada ido sau daya Imaan ta dauke kanta ta wani tamke fuska, ita ma Safeenar haka tayi tana jin wani mugun tsanar imaan har xuciyarta, Mujaheed ya karasa ya bude dakin dake downstairs yana kallon ciki, ganin Inna na bacci ya rufe ya dawo yana kallon Safeenah da fuskarta ke dauri tana kallon direction daban yace "She is sleeping" kamar jira take ta Juya da sauri ta koma sama, kallon Imaan yyi sai kuma ya bi bayanta, Imaan ta mike a hankali ta tafi dakin da Inna ke kwance ta bude jakarta ta dau dari biyar da ta gani a ciki ta rufe jakar sannan ta fito, kofa ta nufa direct ta fita parlon tana murguda baki, Mai gadi ya tashi ya bude mata gate tayi ficewarta tana ce masa sai anjima yayi mata Allah ya kiyaye, tana isa babban titi ta samu adaidaita ta shiga ta gaya masa anguwarsu. Safeenah na shiga bedroom dinta Mujaheed ma ya shigo ya rufe kofar ya juya yana kallonta yace "Toh girkin fa...." Xaunawa tayi gefen gado tana cire dankwalin kanta dogon gashin ya sauka kasa, a d'an fusace tace "Toh wai ba cewa kayi tana bacci ba, and you brought the idea of asking her first before cooking, plss Mujaheed let me... Sannan gaskiya kada yarinyar nan ta sake xuwa min gidana daga yau, am sorry to say this wllh I dislike her with passion, I don't know why amma gaba daya naji na tsaneta with all my heart" Kallonta Mujaheed ya dinga yi da wani expression, fuska daure yace "You are looking into my face and telling me u dislike my blood, are you on ur right senses Safeenah??? meye damuwar ki da ita, to bari ki ji, ba ki isa ki hana imaan shigowa gidan nan ba tunda ba gidan ki bane.... Kuma ki sakko yanxu ki girka ma grandmum dita lunch" a mugun fusace tace "It's better ka fita ka tafi eatry ka samo masu lunch don wllh wlh baxan yi ba, Banda hauka ma ni na taba jin inda ake tilasta amarya sai ta yi girki on her third day a gidan miji, to baxan yi ba, ka fita ka siyo masu ko kasa blood din taka ta girka" tana kai wa nan ta mike a fusace ta tafi can karshen gado ta xauna, shi dai kallonta kawai yake trying hard to control his temper, underneath his breathe yace "I will treat ur f**kup soon" daga haka ya fice daga dakin, ta bi sa da harara murya can kasa tace "Xaka san blood din ka ce" Mujaheed na sauka downstairs ganin Imaan bata parlor ya tafi kitchen nan ma bai ganta ba, dakin da inna ke kwance ya shiga nan ma bai ganta ba, Inna ta d'an bude ido cikin muryar bacci tace "Azahar yayi Mujaheed?" Yace "Imaan fa?" A firgice ta mike xaune tace "Wacece kuma Imaan" bai ce komai ba ya fito dakin ya tafi compound nan ma bai ga alamanta ba, juyowa yayi da mamaki xai dawo parlor ya kusa cin karo da Inna tana xaro ido tace "Ina take?" Yace "Yanxu na sakko ban ganta ba" salati Inna ta saki ta fashe da kuka tace "Ai ni na shiga uku daga fito da yar mutane ta min rakiya ta 6ata, toh Ina ta shiga Mujaheed, ka rufa min asiri ita kenan Allah ya ba Bukar, har a koma ga Allah Bukar baxai taba yafe min ba wllh, ka cece rayuwata Mujaheed a nemo ta" Wani kallo Mujaheed ya dinga yi mata ta bangajesa ta nufi gun mai gadi da gudu tana hawaye tace "Yaro wata yarinya fara yar doguwa siririya kamar xata karye ta fita ta get din nan daxu??" Mai gadi yace "Ehh ta fita, har ma mun yi sallama" Inna ta saki wani dogon salati a rude tana tafe hannu tace "Amma kai d'an banxa ne sakarai gantalalle, ya xaka bar yarinya ta fita bayan tare kaga muka shigo, ita kenan fa gun uban a duniya, mutane dai ba tsoron Allah, ya bar yar mutane ta fita ta shiga gari, yanxu ta ina xan fara nemo Imaan ni patuu, ya ubangijina ka dubeni....." fashewa tayi da kuka ta fice daga gate din da gudu ko Hijabi babu, Mujaheed dai ya koma ciki ya dauko makullin mota ya fito ganin har Inna ta fice ya bude motar yyi warming dinsa Mai gadi ya bude masa gate ya fita, kafin Inna ta isa titi ta tare mutane sun fi biyar a hanya tana masu describing din Imaan ko sun ganta, duk aka ce mata ba a ganta ba sai ta rushe da matsanancin kuka tana cewa "Bukar baxai ta6a gafarta min ba har duniya ta nade" hakuri aka dinga bata tana tafiya tana kuka har ta isa titi, Parking Mujaheed yyi ya sauke glass, ya wani daure fuska yace "Shigo mu wuce" a fusace ta kallesa tace "In wuce gidan ubanwa ba yarinyar mutane, gidan ka dai ya xama na jaraba daga xuwa Imaan ta 6ata...." A fusace yace "Wai imaan din yarinya ce da xaki tsaya titi kina nemanta?" Ta xaro ido tace "Yarinya ce a gun ubanta wlh, ita kadai fa garesa, wllh ba ruwana ka rabu da ni Mujaheed, me xanje ince ma Bukar da Aisha idan na shiga mota...." Sai kuma ta rushe da kuka mai ta6a xuciya, ganin mutane an fara taruwa kanta Mujaheed ya ja tsaki yaja motarsa ya bar ta wajen, gida ya wuce direct, yana parking kofar gida ya shiga ciki, babu kowa compound din ya tafi part din su Imaan, ya kusa minti daya tsaye a balcony kafin yyi sallama murya can kasa ya bude kofar ya shiga parlon, imaan ce xaune parlon da plate din abinci gabanta tana ci tana kallo, suna hada ido ta mike da sauri har tana tuntube ta nufi dakinta da gudu ta shige ta kulle kofa, Ammi ce ta leko daga kitchen, yyi kasa da kai yace "Ina yini Ammi" tace "Lafiya lau, ya gida" yace "Alhmdllh" komawa kitchen tayi ya xauna saman kujera a parlon, ba a dau lkci ba Ammi ta fito tace "Ya amarya fa..." ya d'an yi murmushi yace "Tana lafiya" tace "To maa sha Allah, a xubo maka abinci?" Yace "A'a Alhmdllh" dauke abincin da imaan ta bari a parlon tayi ta kai dinning ta ajiye ta dauko wani plate ta rufe, Ammi tace "Ka dawo da Innar ne?" Yace "A'a, tana dai tahowa" Bai rufe Baki ba sai ga Inna duk ta hada xufa tace "Ina Bukar yake?" Ammi na kallonta da mamaki tace "Sannu da xuwa Inna" Inna tace "Ke tambayar ki nake Ina Bukar, ban ga imaan ba wllh..." Ammi tace "Imaan kuma, ae ta dawo tun daxu" salati Inna tayi a hankali tana tafe hannu tace "Ta dawo?? Amma wannan 'ya ta Bukar axxaluma ce wllh, Allah kaga yanda yarinyar nan ta daga min hankali na dinga tona ma kai na asiri a titi, Allah kaga yanda ta sa na bar jakata da dubu daya a gidan mutane na fito ba shiri, Allah kaga yanda ta sa cikina ya rude a titi na dinga neman bayan gida...." Sai kuma ta rushe da kuka ta fita parlon tana cewa "Bukar dai ya haifi jaraba, don imaan jarababbiya ce, ko da yake uban nata ma fitinanne ne" Ammi dai banda murmushi ba abinda take, ta kalli kofar dakin imaan tace "Imaan" sai da ta kirata sau biyu sannan Imaan ta yi ma Sadeeq sallama a wayan da suke yi, ta fito da hijab har kasa tana sunkuyar da kai, Ammi tace "Meyasa kika taho baki sanar da Inna ba?" Kamar xata yi kuka tace "Ammi bacci fa take ta yi, kuma ni na gaji ina son dawowa gida" Ammi tace "Toh ai kin kyauta" Imaan ta saci kallon Mujaheed dake ta kallonta, ta juya da sauri ta koma daki ta rufe kofarta. Some days later aka fara shirye shiryen saukan su Imaan a gidan, during this period soyayya mai xafi imaan suke yi da Sadeeq amma ta waya, gaba daya ya ki xuwa ta rasa me yasa sai dai ya kirata, kullum xancensa shi dai ji yake kamar ya jawo kwanakin duk da bai fi saura wata biyu xa su xana jarabawan waec ba, ko da xai xo gidan kuwa dama Inna yake xuwa gaidawa kuma ko ita imaan bata sani sai ya tafi xai kirata yace ai ya xo gidansu, ranan asabar ya kama saura sati daya saukansu, ranan kuma ya kama sati biyu da bikin Mujaheed, misalin sha daya da wani abu na safe ya xo gida tare da Safeenah, ubansun lace ne jikinta sai mayafi da ta sakale a wuya hannunta rike da handbag sai takalmi mai tsini da ta sa, tayi kyau har ta gaji, sai xuba kamshi take, fuskar nan nata ya sha make up ba a cewa komai, part dinsu ya nufa tana biye da shi, su Maimoon da Ummi suka yi welcoming dinta da fara'a, ta amsa masu da siririyar muryarta tana murmushi, Maimoon ce ta tafi sama ta kira Aunty, Aunty na sakkowa tace "A'a Aunty amarya ce a gidan namu, Sannu da xuwa" Safeenah ta kalleta tace "Yauwa..." Aunty ta xauna tace "Fatan an tashi lafiya" Safeenah tace "Lafiya lau ya gida" Aunty tace "Alhmdllh, ya naku gidan" Safeenah tace "Lafiya lau" Aunty tace "Toh madallah..." Mujaheed dai sai kallon Safeenah yake jin bata gaishe da Aunty ba, Bai dai ce komai ba ya kalli Aunty yace "Abba fa?" Aunty tace "Tun safe ya fita" Mujaheed ya mike yace "Ohk bari mu gaida Inna" Aunty tace "Toh shkkn sai kun dawo" yace "Yusuf ya dawo?" Aunty tace "A'a bai dawo ba" kofa ya nufa Safeenah ta mike ta bi bayansa Aunty ta bi ta da ido har suka fita ta girgixa kai ta mike ta je ta ci gaba da abinda take, suna fita Mujaheed ya kalleta rai bace yace "Abinda kika yi kin kyauta kenan Safeenah, mum dita ce ita ma fa?" Tsayawa tayi tana kallonsa da mamaki tace "Me nayi kuma?" Yace "Did you greet her?" A fusace tace "Kai komai kace fada da bala'i, to ni ban ma sani ba, da muka fito sai kayi correcting dina ba ka dinga min fada ba haba" Bai tanka ta ba ya ci gaba da tafiya ta bi bayansa tana tabe baki, part din su Imaan ya shiga tana biye da shi tace "Nan ne part din innar?" Ya kalleta yace "Part din uncle dina" Bai jira cewarta ba ya shiga parlon da sallama, d'an tsaki tayi ta shiga ita ma, Ammi na xaune parlon ta mike ganinsu tana masu sannu da xuwa da fara'a, Mujaheed ya xauna ya gaisheta ta amsa tace "Sannun ku da xuwa" Safeenah da kallo daya tayi ma Ammi ta gane ita ce Mahaifiyar Imaan coz it's soo obvious, ta wani daure fuska tana kallon Tv, Ammi tun da ta kalleta sau daya taga bata gaisheta ba dama bata sake kallonta ba, ta tafi kitchen tana cewa "Bari in kawo maku ruwa" wani kallo Mujaheed ya dinga yi ma Safeenah da ta bude jaka ta fiddo chewing gum ta 6are ta jefa a baki tana tauna, murya can kasa tace "Did you greet her Safeenah?" Banxa tayi masa tana taune taunenta, Ammi ta fito ta ajiye ruwan kusa da shi, Yana kirkiran murmushi yace "Ae daga gida muke ma" Ammi ta xauna tace "Ae ruwa ne" daukan bottle water daya yayi yace "Daddy fa?" Ammi tace "Yana Abuja" Mujaheed yace "Toh xa mu je gaida Inna yanxu" Ammi tace "Toh maa sha Allah, nagode kwarai" mikewa yyi ya nufi kofa Safeenah ta mike ta bi bayansa Ammi ta bi ta da kallo, sai da suka sauka balcony ya juya yana kallonta kafin yace komai ta wuce sa da sauri tana kas kas da cingam fuska daure, gyada kai yyi ya dau hanyar part din inna ta bi sa a baya tana kyabe baki, Inna na share parlornta ta daga kai tana kallon Mujaheed tace "Waye wannan" Bai tanka ta ba ya cire takalmi ya shiga parlon, Safeenah ta cire takalmanta tana kirkiran murmushi tace "Sannu da aiki Inna, kawo in karasa share maki" Inna tace "A'a bar shi yi wucewar ki ciki, daga xuwa kuma sai ki hau shara ba ruwana, balle ma na gama" tace "A'a don Allah ki bari Inna, ki kawo in karasa" ajiye tsintsiyar Inna tayi ta mike ta amshe jakar hannunta tace "Toh ai nagode dama bayana kamar xai cire wllh, ita wancan mata tana kwance daki wai ba lafiya, dadin abun ma an san bata da lafiya kafin ta taho nan balle ace a parlon Inna, shi sa ban wani gigice ba, Allah dai ya yaye mata wannan bala'i da ba a san kansa ba....." Mujaheed sai kallon Inna yake sannan ya kalli kofar dakin bai dai ce komai ba, Safeenah ta gama tattare parlon ta kwashe dattin da bai taka kara ya karya ba a Parker sannan ta mike tana murmushi tana kallon Inna tace "A Ina xan xubda dattin?" Inna tace "Can bayan window xaki tafi kwandon sharan yana nan xaki gansa fess na wanke wllh sai a iya xuba tuwa a ciki a ci, sai ki xuba a hankali kar ya bata jikin kwandon har hypo na sa yayin wankewa" Safeenah ta fita parlon ta sa takalminta mai tsini ta wuce bayan window, Mujaheed na kallon Inna da sauri yace "Me ya sameta?" Inna na kakkabe kujera tace "Wai Imaan, toh ga ta nan dai ya dama da xaxxabi ta tashi, ko ina ciwo sai ga al'ada shi ma ya xo ya sa ta gaba, daxu ta gama sharban kuka a nan, duk babu inda bata mirgina ba a parlon nan, ni dai baranda na koma nayi xamana ba ruwana, to nace ta tafi gidansu ta ki tafiya ya xan yi da ita...." mikewa yyi da sauri tace "A'a kar ka tasheta ka rufa min asiri, daxu wannan d'an albarkan Bulasawa ya xo dubata ya taho da magunguna da allurai...." Tsayawa Mujaheed yyi yana kallonta, Safeenah ta shigo parlon ta xauna kasan rug tace "Ina yini Inna?" Inna na murmushi tace "Lafiya lau 'yar nan, amma ku daina cika powder a fuska, kin dai yi kyau wllh powdern ne yyi yawa har kina naso..." Sunkuyar da kai Safeenah tayi tana ta kirkiran murmushin karfin hali, Mujaheed xai shiga daki Inna tace "Kinga fitina ko, Mujaheed nace kar ka tasheta, wllh allura aka mata ta samu bacci, ya xan yi da raina idan ka tasheta yanxu?" Bai tanka Inna ba ya shiga dakin, Safeenah na kallonta da sauri tace "Waye ba lafiya?" Inna ta marairaice tace "Wllh imaan, kamar baxata yi ba yau, nace kar ya tasheta ya ki saurarata, duk ya rikice...." Mikewa Safeenah tayi da sauri tace "Subhanallah bari in masa magana" daga haka ta shige dakin. *Imaan isn't for free* it's 300 via Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah Then u show ur evidence of payment via my WhatsApp number 07087865788Gefen Imaan dake bacci Mujaheed ya xauna a kan gadon Inna ya kai hannu forehead dinta yana kallonta, Bude ido tayi a hankali, ya ta6a jikinta xai yi magana Safeenah ta shigo dakin kamar an hankadota, rike kugu tayi tana kallonsu, duk da mamakin ganinta da Mujaheed yyi bai nuna ba ya dauke kai daga kallonta, Imaan ta mike xaune da kyar ta wani daure fuska, Mujaheed na kallonta murya can kasa yace "Wani maganin kika sha?" Magungunan da Sadeeq ya kawo mata daxu ta nuna masa, ya duka ya dau ledan ya fiddo drugs din yana kallonta yace "Wa ya kawo maki?" Shiru tayi ta ki cewa komai, ya hade rai yace "Am asking you" turo baki tayi ta koma ta kwanta, Safeenah dai sai kallonsu take rike da kugu, Inna ce ta shigo dakin tana kallon Safeenah tace "Safara'u kike ko wa, ba kya fita parlor ki bar su suyi sirri ba, kinsan fa komai nata ya sani, yanxu ganin ki sai ta ji kunyar gaya masa har da ciwon mara a abinda ya dameta, don Allah ki dan koma daga parlo" Safeenah dai bata ce komai ba sai murmushin karfin hali take tana sunkuyar da kai, Inna tace "Ae ba wani abu bane, bbu abinda Mujaheed bai sani ba na Imaan, yanda kika san Yaya mace haka ta mayar da shi tun bata kai haka ba...." Juyawa Safeenah tayi ta nufi kofa ta fice Inna ta bi bayanta tana waigo imaan tace "Dama ki rufa min asiri kar ki bata min xanin gado ki cuce ni, ba kowa gareni ba da xai wanke yanxu Mujaheed ba gidan yake ba" D'an murmushi Mujaheed yyi har inna ta fita, Can ya wani hade rai yana kallon Imaan yace "Wato kiran saurayin naki kika yi kika ce masa baki da lafiya koh?" Kamar xata yi kuka tace "Ni bani na kirasa ba yaya" fuska daure yace "Toh wa ya kirasa" a hankali tace "Inna" yace "Wa ya kira mata shi?" Imaan tace "Ni ban sani ba ina daki" Ya kara hade rai yace "Shine kika ce masa kina period koh?" Xaro ido tayi tace "Wllh ni ban ce masa ba Inna ce ta fada masa nima ai sai da naji kunya fa" tana magana tana turo baki, yace "Toh wa yayi maki alluran?" Shiru tayi, ya d'an mata tsawa yace "Answer me now" turo baki tayi tace "Inna ta min" sai kuma ta rufe fuskarta da sauri a pillow tana dariya a hankali, kallon ta ya dinga yi yana jin xuciyarsa na wani tukuki, a hankali ta dago tana kallonsa, ganin yanda ya daure fuska ba shiri ta shiga taitayinta strictly yace "Sai kika bude masa kaya ya maki allura yana kallon ki right?" Sosai ya bata dariya amma bata yi ba tana komawa baya a hankali tace "Ni a cinya nace ya min, kuma a nan ya min fa yaya, bari in nuna maka wajen ma" tana fadin haka ta dage gown din jikinta a hankali tana nuna masa lap dinta, a hankali ya sauke idonsa yana kallon fresh lap din nata, lkci daya yaji ransa yayi wani mugun baci xuciyarsa na tafarfasa, tayi murmushi ta rufe kafan tace "Kagani ai" fuska a tamke yace "When xa ku fara exams na first term?" Ta buda manyan idonta tace "Saura kusan four weeks ai Yaya" yace "Good ana gama saukan ku dama idan Inna xata taho gidana ku taho tare" ta xaro ido tace "Saboda me Yaya?" A tsawace yace "I am giving you instruction, don't question me" daga haka ya mike ya juya ya nufi kofa rai bace, ta bi sa da wani kallo bayan ya fita, murya can kasa tace "Tabb, waye xai je gidan ka, ni dai baxan je ba" Xaune ya tadda Inna kan tabarma ta daura kafa daya kan daya tana ba Safeenah labarin irin wahalan da tayi da Mujaheed tun daga ranan da aka haifo sa duniya.... Inna na kallon Safeenah da kyau tace "Ko ke baki ga bakin d'an tsut ba??" Duk da irin yanda Safeenah ta dinga dakewa coz at first she wasn't interested with the story gaba daya hankalinta na daki ganin Mujaheed bai fito ba har sannan, amma bata san lkcn da ta fashe da dariya ba har da sakkowa kasa tana kallon Inna, Inna ta hade rai tace "Ke Safara'u ba batun dariya ba wllh, ya tsotsi uwar ne ba kadan ba sai dai Allah ya bata lada, sai kin gansa wani narkeke da shi malam, don dama nonon Rukayya ba dai kyau ba gaskiya" Dariya kawai Safeenah take har da kyakyatawa, Inna ta tabe baki tace "Uhn ni dai ba ruwana" Mujaheed dai yayi still bakin kofar daki ya kasa karasowa cikin parlon, Inna tace "Toh wllh da ya dawo wajena yana da shekara uku sai...." Katse ta Mujaheed yyi fuska daure ta hanyar ce ma Safeenah "Tashi mu tafi" ita dai sai dariya take, Inna tace "Ya haka ina bata tarihi Mujaheed" Mujaheed yace "Toh sai ki jira idan an baki mai gadin gidan tarihi...." Inna tace "Meye laifina Mujaheed, matar ka ce fa kuma sai mu xauna tana kallona Ina kallonta kamar kishiyoyi" Mikewa Safeenah tayi tana dariya tace "Toh Inna mu xa mu koma xan xo ni kadai in sha Allah sai ki bani karshen labarin" Inna na washe baki tace "Toh Safara'u shiga ku yi sallama da Imaan din kiyi mata Allah ya sauwake" D'an dariyar dake fuskar Safeenah ya dauke bata dai ce komai ba ta shiga dakin, tsayawa tayi bakin kofa tana kallon Imaan dake xaune saman gado from head to toes, imaan ta wani daure fuska, Safeenah ta ja tsaki tana yatsine fuska ta fice daga dakin. Dai dai nan aka yi sallama bakin kofa, Inna ta mike da sauri tana amsawa tace "Bisimillah Bukar, Mujaheed ne kadai da amaryarsa, shigo" Sadeeq ya shigo parlon yana murmushi, hannu ya mika ma Mujaheed dake tsaye bakin kofa yana kallonsa, Mujaheed ya amsa still looking at him suka gaisa, Inna na washe baki tace "Toh xauna Bukar" Xaunawa Sadeeq yyi kan lallausan rug dake parlon, Inna na kallon Safeenah tace "Saurayin imaan kenan Safara'u, tana gama sakandari nan da wata daya xuwa biyu dama xa a fara maganar auren su, baki ga ba yaro mai kirki da sanin ya kamata wllh" Safeenah tana kallonsa tace "Sannu da xuwa" Sadeeq ya mata godiya yana murmushi, Safeenah ta nufi kofa tana kallon Mujaheed sannan ta kalli Inna tace "Toh Inna bari mu je sai na sake dawowa" Mujaheed yayi ma Inna sallama ya fita Safeenah na biye da shi, sai da suka d'an yi nisa ya tsaya yace "Ki tafi bangaren mu ki jira ni, I forgot i need to discuss something with grandma" da mamaki ta dinga kallonsa, can tace "Toh sai mu koma tare ai" ya wani hade rai yace "Wannan sirrinmu ne, do as I say plss" Bai jira cewarta ba ya juya ya koma parlon Inna, ta bi sa da kallo da mugun mamaki, Inna ta xubo ma Sadeeq abinci ta cika masa nama tam ta ajiye gabansa xata dauko ruwa kenan Mujaheed ya shiga, cike da damuwa tace "Naga abinda ya isheni.... mai ya dawo da ku kuma Mujaheed ba kun tafi ba, wllh shi kadai na ma girkin ban da ku...." Sadeeq bai san lkcn da ya fara dariya ba, Mujaheed ya wani hade rai yana kallonta, tace "Ni dai ba ruwana, mutane dai ba gaskiya meye kuma na dawowa bayan mun yi sallama kun tafi" Mujaheed bai fasa karasawa cikin parlon ba ya xauna, Inna ta ajiye ma Sadeeq ruwa da malt biyu tace "Toh ni ban san yanda xan yi da kai ba gaskiya Mujaheed, ko in jiko maka garin kwaki ina ma da gyada wllh" Sadeeq ya hadiye dariyarsa yace "Wllh Kaka ya min yawa xa mu ci wannan tare" Inna ta tsuke fuska tana kallon Mujaheed tace "Katon ba sai ya cinye gaba daya ba kana xaune Bukar...." Sadeeq na murmushi yana kallon Mujaheed da ya hade rai yace "Bismillah Dr" Mujaheed yace "Alhmdllh, I am okay" Inna tace "To maa sha Allah, maxa maida hankali ka cinye kayan ka Bukar, Ni dai nasan sai ka fita xai tsigaleni tass.... Toh wannan duk bai dameni ba tunda Allah ya ga xuciyata kai na ma girki, ban san da xuwansu ba" Sadeeq couldn't stop smiling ya dau spoon ya debi abincin ya kai baki bayan yayi Bismillah, Inna ta xauna tace "Ita ma imaan d'an kadan na debar mata gashi can rufe a kitchen, toh ni basu sanar min xa su xo ba da nayi girkin da su, meye a ciki don dai ka ba mutum abinci, kawai fa ganin mutumi nayi gantsantsan a kaina mata na tsaye bayansa, na ja bakina nayi shiru na basu hanya, shi sa na tafi kitchen na adana maka abincin ka kada su gani su tafi da ni a baki suce na masu rowa, kasan mutumin yau" Mujaheed dai bai tanka ta ba, ta gaji da xubanta tayi shiru, yana ta xaune har Sadeeq ya gama cin abinda xai ci, bayan Inna ta tabbata da gaske ya koshi ta kalli Mujaheed tace "Toh don Allah kayi hakuri ka ci sauran, kaga dai a nutse ya ci abincin irin na yan gayu" Sadeeq ya fara dariya ya kasa kallon Mujaheed dake kallon Inna ba yabo ba fallasa, Inna ta tabe baki ganin Mujaheed bai ce komai ba ta dauke abincinta ta wuce kitchen ta rufe, dawowa tayi tana kallon kofar daki tace "Toh imaan dakin xai bi ki fisabilillahi, ki fito mana" sai da Inna ta kara magana imaan ta fito da hijab, Sadeeq ya dinga kallonta, rakubewa tayi jikin kujera tana kallonsa a hankali tace "Ina yini" yayi murmushi yace "Lafiya lau, how are you feeling now" tace "Na ji sauki" yace "Maa sha Allah, hope you've eaten?" Ta gyada masa kai, Inna dai sai kallonsu take tana murmushi, imaan ta saci kallon Mujaheed dake kallonta fuska daure, Dauke kai tayi da sauri, Sadeeq yace "Toh shkkn kaka na cika alkawari tunda na dawo na ci abinci, ni xan koma" inna tace "Wllh na ji dadi Bukar Allah maka albarka, tashi ki raka sa ke" Kudi ya fiddo aljihunsa dubu ashirin ya ajiye kasa kan carpet da ya tashi yace "Kaka tukuicin girkin, naji dadi kuma nagode" Inna tayi tagumi a hankali tace "Naga abinda ya isheni... Bukar dai baya gajiya, abincin ma sai an bada tukuici?? Toh Allah maka albarka, ni dai na gode baxan tsaya ina jayayya da kai ba kamar karamar yarinya, nagode" Yana murmushi ya nufi kofa, Inna na kallon Imaan ta hade rai tace "Ke dai sususu ce wllh, baxa ki tashi ki rakasa ba toh" imaan ta turo baki ta mike ta bi bayansa, Inna na kallon Mujaheed tace "Toh kullum aikin kenan fa wllh, sai ya ajiye min damin kudi haka kafin ya fita har na rasa yanda xan yi da kudi a dakin nan, ni fa ya fi min mutane da dama a duniyar nan don yasan abinda ya kamata, ku ma dai ku ji tsoron Allah ku dinga koyi da shi..." Mikewa Mujaheed yyi ya fice daga parlon. Tsaye Mujaheed ya tadda su kusa da flower sai wani sunkuyar da kai imaan take shi ko sai kallonta yake kamar lkcn ya fara ganinta, kamar mai counting steps dinsa ya dinga tafiyar don basu lura da shi ba, murya can kasa Sadeeq yace "Plss ki kalleni dear let me feel relieved, I've missed you alot, but staying far away from you and just listening to ur voice is d best to me" Ita dai ta kasa dago kanta, a hankali ya kamo hannunta ta dago manyan idanuwanta tana kallonsa, yyi murmushin sa mai tsuma xuciyar wanda ya gani cikin cool voice dinsa yace "I love you Imaan, I am always dreaming to be with you by my side as my wife.... I wish xa ki ga yanda na kagu ki xama matata.... I just can't..." Sai kuma yyi shiru ya lumshe ido, Imaan tayi still ganin Mujaheed da ya tsaya yana kallonsu, da sauri ta xame hannunta daga na Sadeeq, Mujaheed ya dauke kai ya ci gaba da tafiya gently, Ko Sadeeq bai juya ba yasan shi ne, kuma ya ki kallonsa, har sae da Mujaheed yyi nisa sannan Sadeeq ya bi sa da wani kallo, can ya gyada kai smiling, Imaan tace "Xan je in kwanta na gaji" yace "Sure dear, hope cramps din yyi sauki?" Xaro ido tayi sai kuma ta rufe fuska da sauri, ya dinga kallonta yana murmushi, ya kai bakinsa kusa da kunnenta a hankali yace "A day will come da xaki san kunya baxae amfane ki ba" turo baki tayi har sannan ta ki kallonsa, murya can kasa yace "I want just a favor from you... And don't deny me plss" tana kallonsa tace "Na me?" Yana murmushi yace "I will text it to you idan na shiga mota ynxu coz I am not ready to dig u out from underground now" xaro ido tayi tana kallonsa, ya hade rai yace "And if you deny me, I won't be happy imaan" Bai jira cewarta ba ya fara tafiya yace "Expect the text now, gobe I might come in the evening in sha Allah" ta bi sa da kallo har yyi nisa sannan ta juya a sanyaye ta koma part din Inna. Bayan magrib imaan na xaune dakin Inna bayan ta gama shirin bacci xata kwanta ta tuna wayarta da text din da Sadeeq yace xai turo mata tun da rana, mikewa tayi da sauri ta dau Hijab ta saka ta fito parlor tasan ma kila yana ta kiranta, Inna dake xaune parlon tana cin abinci ganin ta nufi kofa ta tabe baki tace "In ji baki mance komai naki a dakina ba Imaan" imaan tace "Xan dawo fa, wayata xan je in dauko a gida" cike da damuwa Inna tace "Me kuma xa ki dawo ki min?? Tun safe fa kike nan" Imaan bata saurareta ba ta fita parlon, daga nisa ta hango mutum na tahowa kamar Yusuf kamar kuma Mujaheed, duk da Yusuf ta san ya daina xuwa part din Inna sai tare da Abba, Tsayawa tayi har sai da ya iso kusa da haske taga Mujaheed ne, turo baki tayi ta juya da sauri ta koma part din Inna, Inna da ta bar abincin da take ci ta tafi tana share dakinta ta daga kai tana kallonta tace "Naga jaraba... Har kin dawo??" Imaan ta bi ta gefenta ta shige dakin tana cewa "Ko ba Yaya bane" Inna ta ci gaba da sharanta tace "Toh dama ki kakkabe min xanin gadona ki gyara gadon fess ni ba gantalalliya bace, ba haka nake barin dakina ba in kwana tare da wari" Inna ta mike ganin Mujaheed tace "Wannan shine anyi ba ayi ba, yanxu kayi auren ma baxa mu sarara ba Mujaheed kullum kai ta mana sintiri a gida, ba daxu da rana ka xo ba to me kuma ya dawo da kai, ko akwai ajiyar ka a parlon nan ne baka dauke ba har yanxu" Bai tanka ta ba ya nufi kofar dakin ya bude ta bi sa da kallo baki bude, imaan ta koma can karshen gado kamar xata yi kuka tana kallonsa, Ya wani mugun daure fuska yace "You had better keep on running away from me coz wllh wlh am promising you this... if I should get hold of you I won't take it likely with you.... I will seriously deal with you" a fusace Inna tace "Naga abinda ya isheni, don Allah Mujaheed ka rufa mana asiri, me ta maka kake kunduma mata xagi haka, yarinyar da kamar baxata yi ba daxu Allah ya rufa mana asiri Bulasawa ya rufa mana ya mata allura ya bata magani taji sauki shine yanxu xaka xo kana xaginta kana nuna ta da yatsa kana gaya mata maganganu marasu dadin ji, to ni dai ba ruwana ka tafi ka ba mu waje, ni na ta6a jin inda aka aurar da mutum kuma yyi ta sintirin dawowa gida kamar dai da ajiyarsa da ya mance bai dauka ba, ni dai gaskiya na gaji da kai kar ka sake xuwa min, tunda kayi auren ka kayi xamanka a gidanka ka bar min jikata ta sarara...." Kawai Inna gani tayi ya shige dakin ta fasa ihu tana kwala ma Ahmadu kira iya karfinta, ba kuma wanda xai ce ba wani mugun abun ta gani ba, Imaan ma duk ta rude xata gudu bandaki ya fixgota kawai sai ji tayi xabga mata mari mai lafiya, ta rike fuskarta a gigice, inna na ganin haka ta fice da gudu xuwa waje tana kiran Abba, Mujaheed na kallonta da idonsa da suka kada cikin harshen turanci yace "Muharramin ki ne mutumin nan da kika mika masa hannun ki ya kama, dama iskancin da ku ke yi da shi kenan, yana tsaye kusa da ke kamar xai shige jikin ki kina jin dadi koh? To wllh yanxun nan xan je in sami daddynki in sanar masa komai" a rikice imaan ta rikosa ta dinga basa hakuri tana cewa "Yaya ni bani nace ya rike ni ba, don Allah kayi hakuri baxan kara ba wllh, don Allah kayi hakuri" sosai xuciyarsa ke tafarfasa yana kallonta, ta hade hannayenta hawaye na sakko mata tace "Don Allah kayi hakuri baxan kara ba da gaske Yaya" tana fadin haka ta boye fuskarta a jikinsa tana kuka, har ransa yake jin kukan nata, Bai san lkcn da ya jawota jikinsa ba cikin sanyin murya yace "That's very wrong imaan, I've told you times without numbers... that guy is just here to ruin ur life, to cause you heartbreaks, he is after ur body... He is..." Kasa ci gaba yyi don sosai ransa ke tafarfasa, imaan dai sai sauke ajiyar xuciya take tana kuka a hankali bata ce komai ba, nan ko ko kiris bata yrda da abinda Yayan nata ke fada ba don ita tasan Sadeeq na sonta kamar yanda ita ma take sonsa fiye da xaton mai karatu, dago kanta yayi yana kallon kwayar idonta da ya rine murya can kasa yace "For my sake xa ki rabu da shi plss Imaan?" Ta fashe da kuka cikin rawar murya tace "Ni dai ina son sa Yaya, kuma ai aurena xai yi..." Kallonta Mujaheed yake ko kiftawa babu xuciyarsa na bugawa, da kyar tace "Kayi hakuri plss Yaya, da gaske Ina son sa, but in sha Allah baxan bari ya sake rike hannuna ba" 🌟⭐⭐⭐🌟assslamun alykum ina bawa masoya littafina imaaan hkrn xasujini shru xan dau hutune xuwa bayan.sallah in allah ya kaemu tnx u fans imaaan inbaki biyaba karki karanta🌟⭐🌟 _Maa Sha Allah, koma wacece ko wanene yayi wannan Broadcast din na sama👆🏻 ya sani.... Da *NI* da *shi/Ita* xa mu hadu gaban Ubangiji, ba fa a kan komai ba sai kan gantalallen Hausa Novel wanda baxai kare mu da komai ba, baxai amfane mu da komai ba ranan gobe kiyama, wanda muke fatan ma ba xunubi muke kwasan ma kanmu ba muke kuma rokan Allah ya yafe mana, wato irin xagi da cin mutunci da mai Broadcast din ya ja min jiya wllh tllh xa ayi mana hisabi da koma wanene, don ni dai na yafe duk xagi da na sha amma mai post din ya sani xa mu hadu gaban ubangijin da ya halicce mu in sha Allah, and that's if he or she believes there is God_ Ni ba fitinanniya ba ni ba mafadaciya ba, ni ba mai sa ido ba, ni ba mai takura ba, amma duk da haka ban tsira ba a media sai an cakale ni na mayar da martanin da bana so dai, duk da babba da hakuri aka san sa amma a dai dinga jin tsoron Allah, mutane dai ba gaskiya basa tsoron Allah, a dai dinga jin tsoron Ubangiji ni ba ruwana.🤦🏻‍♀️ Least I forget akwai wani hoton dake circulating na wata mai pink kaya wai Khaleesat Haiydar, to gaskiya ban san yarinyar ba ayi hakuri a daina turo min ana tambaya ko ni ce don ba ni bace, plsss ba ni bace oo... this is not 2012 I am begging you pple ba ni bace...😟 Ranan da na gama Imaan xanyi attaching pic dina a karshen page din sai ku gani😁 One love fans😍 Imaan isn't for free* it's 300 via Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah Then u show ur evidence of payment via my WhatsApp number 07087865788Saketa Mujaheed yayi har sannan bai daina kallonta ba sai kuma kawai ya juya ya nufi kofa ya fita, ta bi sa da kallo tana share hawayen dake xubowa idonta a hankali, komawa tayi gefen gado ta xauna a sanyaye, ko minti biyar ba ayi da fitar Mujaheed ba Inna ta dawo dakin tace "Tashi mu tafi Ahmadu na kiran ki ya ji ba'asi... Yau in sha Allahu xai mana iyaka da shi, kada ya sake shigo min tunda yayi aure, Ina murna na rabu da shi kuma sai kullum ya wani xo min xalo xalo kamar da ajiyarsa da ya mance min a nan???" Imaan tace "Ni dai ba abinda yayi min fa, kuma bance ki je ki ce ma Abba komai ba, ai ni ce ban gaishesa ba shi sa, kuma na hakura ni dai" Sake baki Inna tayi tana kallonta, Imaan ta mike ta nufi kofa tace "Komai sai ki tafi wajen Abba baki jira kin ji abinda ya faru ba..." daga haka ta fice a dakin ta bar Inna a tsaye. A hankali Imaan ta bude kofar parlon su ta shiga gabanta na faduwa, da ta tuna abinda Mujaheed yace wai xai gaya ma Daddy sai hankalin ta ya tashi, amma ta san baxai ma fada ba kawai tsorata ta yayi, Ammi ce kadai xaune parlor tana kallo, ta xauna kasa a hankali ta gaisheta, Ammi na kallonta tace "How are you feeling?" Tace "Na ji sauki Ammi" Ammi tace "Toh Allah ya sauwake, ga abinci can kitchen idan xa ki ci" ta girgixa kai tace "Na ci a wajen Inna" Ammi bata ce komai ba, hakan yasa ta mike ta nufi dakinta, a hankali ta nufi inda wayarta ke ajiye ta dauka xuciyarta na bugawa don bata san abinda xata gani ba, ta xauna gefen gado ta sauke ajiyar xuciya a hankali, can dai ta kunna wayar tana kallon screen din taga message da missed call a gaban screen din, missed call din ta fara shiga taga na sadeeq ne kuma just few minutes ago ya kirata, bude text din tayi tana dubawa kamar idanuwanta xa su fito, ta maimaita text din ya fi sau a kirga, can ta 6ata fuska kamar xata yi kuka, tafi minti goma a xaune, sai can kuma tayi wa Maryam forward din message din, bayan ta tabbata ya tafi tayi deleting gaba daya a wayar, ta d'an yi murmushi ta mike ta cire Hijab din jikinta ta linke ta kashe wutan dakin ta kwanta. Washegari da ya kasance Monday Imaan ta ji sauki sosai hakan yasa tayi shirin wucewa schl da safe, tana tattara few textbooks dinta da xata tafi da su makaranta taga wayarta dake gaban madubi yyi haske, karasawa tayi ta dau wayar taga text din Maryam ne ya shigo tana requesting ta hau WhatsApp su yi chatting, reply tayi mata da cewa sai ta dawo schl daga haka ta ajiye wayar ta fita dakin. Karfe hudu saura Imaan suka fito schl tare da Mariya dake ta mata labari tun basu fito aji ba, tsaye su ka ga Sadeeq jikin motarsa ya rungume hannu idonsa sanye da glasses, Sosai gaban Imaan ya fadi, Mariya ta wara ido tana kallonsa tace "Ya Sadeeq Drivers fa?" Shi dai bai ce mata komai ba, Kallon Imaan Mariya tayi tana murmushi tace "Sai gobe xan ci gaba Imaan" tuni kanninta biyu shiga mota yayan nasu, Imaan ta gyada mata kai tana d'an murmushi tace "Allah ya kai mu" Har Mariya xata shiga motar sai kuma ta kalli Imaan tace "Baxa ku gaisa da yayana ba" Imaan ta kalli Sadeeq dake kallonta ba ko kiftawa, daga inda take tsaye a hankali tace "Ina yini" ya gyada kai yace "Lafiya lau" daga haka ya xaga ya bude maxaunin driver ya shiga ya tada motar suka wuce. Imaan na dawowa islamiyya that same day taga Miss call din Sadeeq, kasa kiransa tayi da farko don bata san me xata ce masa ba, can dai tayi dialing number a hankali ta kai kunne, yana fara ring ya katse ya kirata, tayi gathering courage tayi picking, murya can kasa tayi masa sallama ya amsa yace "You are ignoring my calls ko" ta xaro ido tace "A'a wllh, bana kusa da wayar ne ai yanxu muka dawo islamiyya, jiya kuma Ina part din Inna wayar kuma na part din mu" yace "Ohk, I tot u where ignoring it shi sa ma ban xo ba yau, ya jikin?" Ta langwabar da kai tace "Na ji sauki" yace "Maa Sha Allah" shiru tayi ta rasa abun cewa, can yace "Did you see my text or u don't just want to talk about it?" D'an murmushin karfin hali tayi tace "Sure I saw it, I... but.. I can try doing as u wish, but I can't perform the action in the text" Dariya yayi yace "Ohk then...." Ta turo baki bata ce komai ba, yace "I will call you later xan fita masallaci" tace "Allah ya kai mu" daga haka ya katse wayar. Ranan Thursday da safe bayan Imaan ta gama shirin boko ta sami Ammi a kitchen a hankali tace "Ammi tunda ba islamiyya yau idan na dawo schl plss Ina son in je in gaida Gwaggwo daga nan sai in kai ma Aunty halima katin sauka" Ammi tace "Jiya ba ce min kika yi Thursday da Friday duk xa ku je islamiyyar ba da yamma?" Imaan ta xaro ido tace "Ance sai Friday morning and evening" Ammi ta tabe baki tace "Toh ki kira daddy ki gaya masa, ai ba ni xa ki gaya ma ba" Murmushi Imaan tayi tace "Ae har na gaya masa jiya da daddare" Ammi tace "Toh Allah ya kai mu" Imaan tace "Ameen" shayi ta hada a cup ta fita da bread da egg dinta a plate xuwa dinning. Tana dawowa schl ranan ko abincin kirki bata ci ba tayi wanka ta shirya cikin bakin abayanta ta sa Hijab har kasa ta fito parlor, Ammi dake kallonta tace "Kar ki kai magrib a hanya Imaan" xaro ido Imaan tayi tace "Ammi ni fa cewa Daddy nayi xan kwana" Ammi tace "Kwana kuma?" Imaan ta marairaice tace "Ehh Ammi na gaya masa, ki kirasa ma" Ammi tace "Toh schl din fa?" Imaan tace "A'a ai nace maki islamiyya xan je da safe da kuma yamma tunda Saturday ne saukan ai" Ammi tace "Ba ruwana ni ban ce ki kwana ba da kin gaisheta ki kai ma Halima kati ki juyo, am I clear???" imaan tayi shiru tana kallonta kamar xata yi kuka, Ammi ta ci gaba da abinda take, a hankali Imaan tace "Toh sai na dawo" Ammi tace "Dama kada ki kuskura ki kai magrib a titi ni dai na gaya maki" imaan ta nufi kofa bata ce komai ba har ta fita parlon. Imaan na isa gidan gwaggwo dama gaisheta kawai tayi tace "Ina sauri xan je gidan Anty Halima in kai mata kati in dawo...." Gwaggwo na kallonta tace "Toh shikenan sai kin dawo, ya saurayin naki Sadeeq?" Yar dariya tace "Yana nan, shi xai kai ni gidan Aunty Halima din ma, amma kar ki gaya ma Ammi fa" Gwaggwo tace "Au tare ku ke shine bai shigo mu gaisa ba" imaan tace "A'a yanxu dai ya kirani yana hanya" Gwaggwo tace "Toh Allah ya kawo sa lafiya, Mujaheed na lafiya da amaryar sa dai koh?" Imaan ta turo baki tace "Nima dai ban sani ba" Gwaggwo tace "Baki je gidan ba kenan" imaan tace "Mun je da Gwaggwo amma matar bata da mutunci, ni dama baxan sake xuwa gidansa ba har abada" Gwaggwo tace "Ikon Allah, toh Allah dai ya kyauta, amma ai babu xancen baxa ki kara xuwa gidan yayanki ba Imaan" Imaan ta dau wayarta dake ring ganin Sadeeq ne ta mike tana kallon Gwaggwo tace "Sai na dawo" Gwaggwo tace "Har ya iso" Kai ta gyada mata, Gwaggwo tace "Toh Allah ya kiyaye, hanya a dai kula kin ji" Imaan ta nufi kofa ta fita parlon, yana xaune mota ta karasa ta bude front seat, kallonta ya dinga yi, a hankali tace "Ina yini" ya d'an yi murmushi yana shafa kansa murya can kasa yace "Lafiya lau Hijab queen, you look beautiful in it always, but yau ma sai kin sa?" Shiru tayi tana kallonsa, Yana mata murmushi yace come in" a hankali ta shiga motar ta rufe ba tare da ta yarda sun hada ido ba, ya tada motar yace "Xa ki kai ma Halima card din first koh?" Ta gyada masa kai, driving yake kamar bai son yi, lkci lkci kuma yana kallonta ta gefen ido, shiru babu wanda yace komai cikinsu har suka isa gidan Aunty Halima after 15 mins ride, ya juya yana kallonta a hankali yace "Be fast Imaan" ta gyada masa kai ta sauka ta nufi cikin gidan ya bi ta da ido, jinginar da kansa yayi jikin mota ya lumshe idanuwansa, can ya bude ya dau wayarsa yayi dialing number ya kai kunne, ana dagawa, cikin cool voice dinsa yace "Selim... I think I am just sorry, I had to disappoint you guys, may be some other times xa ku santa, kawai na fasa deal din" Best dinsa Selim dake sauraronsa da mamaki yace "I don't get you Sadeeq..." Sadeeq ya d'an yi shiru sai kuma calmly yace "I can't bring her to that place, she's more than decent and innocent, though I have neva had bad intention toward her... but, I am sorry for the disappointment, I will compensate this deal for what ever amount you guys will require" Selim yace "You are sick, mu ne ba mu san ciwon kanmu ba ko, mu ne ba mu san ciwon babes din mu ba, what's the use of all this Sadeeq, after necessary arrangements da aka gama ka xo kana kawo mana wani surutu, this is very unusual of you, haka on ur Birthday wai wani she's sick baxata xo ba, wato mu namu Girlfriends din ne pure water....." Sadeeq dai tabe baki kawai yyi bai ce komai ba, Yana jin friends din nasa dake guest inn din nasa suna surutu daga karshe ya katse wayarsa, dialing number Mariya yayi, tana dagawa ya gaya mata wani babban wajen cin abinci da xata je ta jirasa in the next 15 mins, yana gama fada mata ya katse wayarsa. Imaan na fitowa gidan cousin dinta ta bude motar tana kallonsa a hankali tace "Kayi hakuri I kept u waiting" murmushi kawai yyi bai ce komai ba ta shiga motar, tada motar yayi suka bar layin, sai da suka hau saman titi ya kamo hannunta da nufin xai mata magana, ba ita kadai ba har shi sai da yayi shock hakan kuma ya sa ya saketa, har kuma suka isa wajen cin abincin bai ce mata komai ba ita ma haka, ganin motar gidansu a haraban eatry din ya gane Mariya har ta iso, Yana kallon Imaan yayi murmushi yace "Mu je" a hankali ta bude motar ta sauka shima ya sauka ya rufe motar ya shiga gaba tana biye da shi har suka shiga wajen, few mutane ne cikin hadadden wajen, Sadeeq ya hango Mariya xaune tana danna waya ta cakare cikin English wears, ya kalli Imaan dake kallon Mariyar da mamaki ita ma, Ya wara mata ido yace "Mu je" ba musu ta dinga bin sa har suka isa gun Mariya, Mariya da tuni ta hangosa amma bata san tare da Imaan bane ta dai ga mace da Hijab, a xuciyarta kuwa cewa tayi ohhh tot ya Sadeeq ya shiryu gaba daya jin kwana biyu shiru ba ace min ga new catch ba balle mu hadu in gilla mata karya, ashe dai da saura, ko wa kuma aka samu mai hijab har kasa, dariya abun ya bata don ita dai tasan he is not a lover of hijab fa, haushi yake ji yaga mace ta sa hijab sanin da tayi masa da, Suna isa inda take ya ja ma Imaan kujera yana kallonta, Imaan dake kallon Mariya ta xauna, shi ma ya xauna, Mariya ta ajiye wayarta ta fara magana kamar yanda ta saba duk sanda suka hadu da daya daga yan matan nasa, tana murmushi tace "Sannu auntynmu, Yaya yace yau dai sai mun gaisa da future wif......" Shiru tayi da mugun mamaki tana kallon Imaan, can ta kalli Sadeeq amma ta kasa cewa komai xai xare ido take, cikin cool voice dinsa yace "Meet my soulmate, the future mother of my angels in sha Allah...." Mariya was just lost of word, imaan kam ta sunkuyar da kai, a hankali Sadeeq yace "Ko bata maki bane Lil sis?" Mariya na kikkifta ido tace "I don't get this ya Sadeeq, are you for real??" gently yace "Sure, my future wife in sha Allah, Imaan is her name" Tasowa Mariya tayi ta rungume Imaan cike da murna tace "Waow, amma na ji dadi sosai wllh Yaya, but you two neva for once told me, me yasa kuka boye min plss..." Imaan dai tayi murmushi bata ce komai ba, waitress ce tsaye kansu tana tambayar me xata kawo masu, Sadeeq yace "Just drinks" Sadeeq na kallon kanwartasa yace "Toh sake min ita kada ki fadar da ita" dariya sosai Mariya tayi ta sake imaan ta xauna, tana kallonsu so happy, ba a dau lkci aka kawo masu drinks din, Imaan dai sai kallon Mariya that couldn't hide how happy she is, tana mitan irin deceiving dinta da suka dinga yi kullum sai yace mata bai gane imaan ba ashe ma ya fi ta gane ta, Shi dai Sadeeq kallon Imaan kawai yake with affection, sai a sannan yake da ya sanin ma amincewa da yayi xai kai ta guest inn yayi proposing mata gaban gantalallun frnds dinsa da a yanda yake ya ma fi su kamun kai... lol, after the proposal kuma party... party that they will be different type of wines, a must drink... Kawai a gama kalle masa soulmate, lkci daya mood dinsa ya canxa, Mariya ta xuba ma imaan drink a disposable cup ita ma ta xuba ta dauka ta mika ma imaan tana murmushi tace "Here.... Future in-law...." Imaan ta amsa tana murmushi, Mariya ma ta xuba ta fara sha tana kallon Sadeeq tace "You can serve ur self" d'an murmushi yyi ya diba ya fara sha, Mariya na shan drink dinta ta fara imagining to ya ake wannan soyayyar da Imaan, imaan dai da ta sani baxata ta6a yarda Sadeeq yyi kissing dinta ba balle ya rungume ta, toh how is her brother coping, Sadeeq that she know can't do with out that tabbb, tunanin hakan ya bata dariya sosai, to ko ya ake wannan soyayya, Sadeeq ya ajiye sauran drink din hannunsa yace "You two should tell me abinda ku ke so na saukan ku that's on Saturday" Mariya tace "Good, muna komawa gida xan maka list dama, muna bukatan lot lot of thingssss" dariya kawai yayi sanin both abinda ya kamata da wanda bai kamata ba kenan xa a rubuta a list in dai Mariya ce, they spent just 30 mins a eatry din daga nan Sadeeq ya mike yace "It's past six now xan mayar da ita gida" Mariya tace "Ohk then, am very happy at this Yaya, Allah ya sanya alkhairi, plss" yace "Ameen" daga haka suka fita eatry din Mariya na cewa "Plss this shouldn't take too long ooo" Imaan dai taki yarda ta kalleta, Sadeeq dai yyi murmushi yace "Sure just in few months time" Mariya ta dinga murna ita a dole Sadeeq xai auri kawarta, motar gidansu da driver ke xaune yana ta jiranta ta nufa tana daga ma imaan hannu tace "Sai mun hadu islamiyya gobe da safe in law" Sadeeq ya bude ma Imaan back seat yana kallonta, shiru tayi tana kallonsa ita ma, ya d'an yi murmushi yace "You don't worry ki shiga, I don't mind being ur Driver" ta d'an yi murmushi ta shiga motar a hankali, ya rufe sannan ya shiga driver seat ya tada motar ya bar eatry din. Yana driving yace "Gidan gwaggwo xan maida ki ko gida?" Tace "Gida, xan kirata ince na wuce gida" yace "Ohk" suna isa layin ya tsaya 2 houses away, sannan ya bude motar ya dawo baya ya shiga ya rufe yana kallonta, sunkuyar da kai tayi gabanta na faduwa, tsoronta daya kada Mujaheed ace yana anguwar balle ya ganta cikin motar duk da glass din is tinted, Sadeeq yana d'an murmushi yace "I think I don't have to propose in midst of friends, just me and you..." ita dai bata ce komai ba tana kallonsa, ya dauko wani karamin box ya bude yana kallonta, sunkuyar da kai tayi gabanta bai bar faduwa ba, ya ciro ring din ciki wanda ba sai na fadi wani iri bane, lol... ya kamo hannunta yana kallonta ya xura mata ring din, ita dai ta kasa dago kai ta kallesa xuciyarta sai bugawa yake ga kamshin sa da ya cikata, Bata ankara na sai ganin ya hade bakinsu tayi, tunda take bata ta6a tsorata na moment din ba, coz it was something that had never happened to her all her life, lkci daya ta fara turasa hawaye na sauka idonta, bai wani dau lkci ba ya saketa shi ma xuciyarsa na bugawa, daura kansa yyi a kafarta cikin sanyin murya yace "I.. i.. am, I am sorry Imaaan" ja baya tayi hakan yasa ya dagata ta bude motar ta daya side din ta fice daga motar da sauri.... *Imaan isn't for free* it's 300 via Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah Then u show ur evidence of payment via my WhatsApp number 07087865788Imaan na shiga parlonsu ta wuce dakinta direct ta kulle kofa ta fashe da kuka sosai. Bayan kusan minti goma Ammi ta dawo daga part din su Aunty ganin takalman imaan bakin kofa ta shiga parlon ta wuce dakinta, alwala tayi ta dawo parlor tana kallon agogo don har sannan da saura lkcn sllhn bai yi ba, ta kalli kofar dakin Imaan tace "Imaan" Da sauri Imaan dake xaune can karshen gado ta hade kai da gwiwa ta daga kanta, Ammi ta sake kiranta, sakkowa tayi daga kan gadon tana goge idonta duk da hawayen ya ki tsaya mata, ta nufi kofa ta bude ta fito parlor, Ammi na kallonta tace "Yaushe kika shigo?" Da kyar ta bude baki tace "Ban dade ba" shiru Ammi tayi tana kallonta da mamaki, Imaan ta sunkuyar da kai gabanta na faduwa sosai, Ammi tace "Kukan me kike?" Ta girgixa kai tace "A'a ba komai" Ammi ta mata wani kallo tace "Zo nan" sosai xuciyarta ke bugawa ta karasa ta duka kasa tana kallon Ammi tace "Gani" cikin tsawa Ammi tace "What's wrong with you?" Duk yanda ta so dakewa kasawa tayi, ta fashe da kuka sosai, duk yanda Ammi ta so boye tashin hankalinta a lkcn kasawa tayi, Tayi kasa da murya tace "Nace me ya faru imaan, kukan me kike yi, talk to me daughter" Cikin rawar murya tace "Da gaske Ammi ba komai" Ammi ta wani hade rai tayi mata wani tsawa tace "Baxa ki bani amsa ba, kukan uban me kike, me aka maki?" Imaan dai ta kasa cewa komai sai hawaye, mikewa Ammi tayi hakan yasa ta tashi da sauri ta koma baya ta fashe da sabon kuka, tsayawa kallonta Ammi tayi, can ta wuce daki da sauri ta dau wayarta ta shiga kiran layin gwaggwo, ta kira ya fi sau a kirga gwaggwo bata dauka ba, kowa kuma yasan gwaggwo haka take da waya, Ammi ta shiga kiran Halima, bayan sun gaisa Ammi tace "Halima Imaan ta je gidan ki?" Halima tace "Ehh ta xo daxu amma ai ta wuce" Ammi tace "Karfe nawa ta bar gidan naki?" Halima tace "Shidda dai kamar yayi, lafiya Ammi?" Ammi tace "Lafiya lau, Ina tace maki xata daga gidan naki?" Halima tace "Bata koma gida bane Ammi?" Ammi tace "Tambayar ki nake" Halima tace "Tace kila ta wuce gida ko kuma ta tafi wajen gwaggwo" Ammi tace "Toh sai anjima" daga haka ta katse wayar, Gwaggwo ta sake kira har ya gama ring bata dauka ba, ta kuma kira nan ma haka, ajiye wayar tayi ta fito, ganin Imaan bata parlor ta wuce dakinta, jin tana bathroom Ammi ta tsaya, gaba daya hankalinta ya tashi sosai, Imaan na gama alwala ta fito, sosai ta tsorata ganin Ammi, ta sunkuyar da kai a hankali tace "Ammi ba komai fa" Ammi tace "Daga gidan Halima kin koma gidan gwaggwo ne?" Ta girgixa kai tace "A'a" Ammi tayi kasa da murya tace "Toh ki gaya min me ya faru" cikin sanyin murya tace "Ba komai fa Ammi, kawai dai kamar bana jin dadi ne" Ammi tace "Baki jin dadi kuma?" Ta gyada kai, Ammi tace "Ina ke maki ciwo?" Ta girgixa kai tace "A'a ba inda ke min ciwo, kawai dai bana jin dadi" shiru Ammi tayi tana kallonta, can tace "Toh ki yi sllh ki fito yanxu" imaan ta gyada mata kai Ammi ta juya ta fita, har Imaan ta idar da sllh ta kasa daina hawayen da bata san dalili ba, tayi kokarin daina hawayen amma hakan ya faskara, har sannan she is just shock, fashewa tayi da kuka a hankali, ta jinginar da kanta jikin gado. Ammi na idar da sllh tayi ta jiranta ta fito amma shiru, hakan yasa ta mike ita ma gaba daya ta rasa me ke mata dadi, gashi ta kara kiran gwaggwo bata dauka ba tasan wayar na can karkashin pillow, A hankali ta bude kofar dakin ta ganta xaune kan darduma ta jinginar da kai da gado tana bacci, Ammi ta karasa inda take ta duka ta kai hannu jikinta ta ji ba xafi, Bude ido imaan tayi ganinta ta ja baya, Ammi na kallonta ta xauna gefen gadon tace "Tell me what's wrong with you plss imaan" D'an murmushin karfin hali tayi tace "Ammi ba komai fa, i am better now" Ammi ta dinga kallonta kafin tace "Toh fito ki ci abinci" tashi tayi a hankali ta dauke pray mat din ta linke ta bi bayan Ammi xuwa parlor, Ammi ta xuba mata abinci a kitchen ta kirata, Mikewa Imaan tayi daga xaunen da tayi a parlor ta tafi kitchen ta amso abincinta ta dawo parlor ta xauna, Sosai Ammi ke studying dinta tana cin abincin sai dai bata ce mata komai ba, ganin xata je ta ajiye abincin da ko rabi bata ci ba Ammi tace "Dawo ki cinye abincin nan" kamar xata yi kuka tace "Ammi ya min yawa" Ammi tace "Dawo ki cinye na ce" babu yanda ta iya haka ta koma ta xauna tana tura abincin da kyar, har ta cinye taje ta ajiye plate din a kitchen ta dawo parlor tana kallon Ammi tace "Ammi ina son xan kwanta" Ammi tace "Ishan fa?" tace "Ba bacci xan yi ba kawai xan kunna kallo a ciki" Ammi bata ce mata komai ba hakan yasa ta wuce daki Ammi ta bi ta da ido har ta rufe kofa. Ammi dai na ta xaune parlor har takwas da rabi aka yi sallama bakin kofa, amsawa tayi Mujaheed ya shigo parlon, Ammi na kallonsa tace "Sannu da xuwa" Ya d'an yi murmushi ya xauna yace "Ina yini Ammi" Ammi tace "Lafiya lau, ya gida" yace "Lafiya Alhmdllh" tace "kwana biyu?" Yace "Alhmdllh" Ammi na kallonsa tace "Baka da lafiya ne" yar dariya yyi yana shafa kansa yace "Aa, am okay, me kika ga" ta girgixa kai tace "A'a ba komai, a xubo maka abinci" yace "A'a Alhmdllh" shiru yayi yana kallon movie da ake yi a tv, can ya kalli Ammi yace "Abba yace Imaan ta je" Ammi tace "Ohk, tana ciki Ina jin ta kwanta, let me wake her" ya kalli agogo sannan ya kalleta yace "Bata da lafiya ne?" Girgixa masa kai Ammi tayi tace "She's ohk" Ammi na kallon kofar dakinta ta kwalo mata kira, ta kirata yyi sau uku amma shiru, can Ammi ta mike ta tafi dakin, kwance ta ganta ta rufa da duvet, Ammi ta karasa ta cire duvet din da sauri Imaan ta rufe idonta, da mamaki Ammi ke kallonta tace "Imaan kina son in bata maki rai a gidan nan yau ko, baxa ki gaya min meye damuwarki ba, wani abun ya faru ne baxa ki gaya min ba" Imaan taki yarda su hada ido ta mike xaune tana goge guntun hawayen idonta a hankali tace "Ammi kiyi hakuri ni nace maki ba komai fa" Ammi tace "Wani abun ya hada ki da gwaggwo ne" Imaan tace "A'a ni ban ma dade a gidanta ba, Ammi it's just mood swings" Ammi tace "Toh xan kira daddyn ki yanxu kuwa in gaya masa, don baxan yadda ki sa min ciwon kai ba ina xamana, wannan ai walakanci ne, ke yarinya ce xaki xauna kina kuka ki ki fadin matsalar ki kice min mood swings, ko iskancin ki na da ne xai dawo yanxu, kuma ki tashi ki fita Abba na kiran ki...." Juyawa Ammi tayi rai bace ta fita a dakin tana mamakin hali irin na Imaan, tasan ko da rufeta xata yi da duka ta dage a kan sai ta gaya mata kukan me take to taurin kanta baxai taba bari ta fadi ba, ita kanta taurin kan Imaan na damunta ne ba kadan ba, parlor ta koma ta xauna tana kallon Mujaheed tace "I don't know what's wrong with her, tun daxu take kuka, na tambayeta meye matsalar ta taki gaya min, kuma kukan na iskanci ne da jin dadi, dama ranta a bace ta bar gidan tunda nace kar ta kwana inda xata je...." Mujaheed na kallon Ammi yace "Kuka kuma" Bude kofar dakin Imaan tayi ta fito kanta a kasa, Mujaheed ya dinga kallonta har ta karaso cikin parlon ta xauna kasa tace "Ina yini Yaya" yace "Lafiya lau, what's wrong?" Kin cewa komai tayi, Ammi sai kallonta take, can kuma dai ta tashi ta wuce daki, Imaan ta hade kai da gwiwa, ya mike ya dawo kusa da ita ya durkusa yana dubanta yace "What happened imaan, an maki wani abu ne?" Ta dago kanta ta wani turo baki tace "Ba komai" shiru yyi yana kallonta, can yace "Tashi mu je Abba na kiran ki" Mikewa tayi shima ya tashi ya nufi kofa ta bi bayansa. Sai da suka yi nisa ya juya yana kallonta da kyau yace "Baxa ki gaya min kukan me kike ba" tace "It's just mood swings" Bata jira cewarsa ba tayi wucewarta ya bi ta da ido, can dai ya bi bayanta, Xaunawa parlon Abba tayi bata yadda sun hada ido ta Abban ba ta gaishesa ya amsa yace "What did you want for ur Qur'anic graduation?" Shiru ta d'an yi, can tayi murmushin karfin hali tace "Abba kawai a min abinda aka ma su Maimoon" yace "To maa Sha Allah, you can go" Mikewa tayi ta masa sai da safe ta nufi kofa Mujaheed ya bi ta da ido har ta fita, wanka imaan tayi bayan ta koma part din su, tana saka kayanta text ya shigo wayarta ta kalli screen din, dauke kai tayi ganin Sadeeq ne ya turo sakon ta karasa shirinta ta bar wayar nan gaban madubi ta kashe wutan dakin ta kwanta, ta jima bacci bai xo mata ba sai juye juye take daga karshe dai baccin ya dauketa. Washegari Friday duk da ynda imaan ta dinga jin ciwon kai haka ta shirya ta wuce islamiyya, karfe sha daya kuma ta dawo gida, har sannan dai bata wani dawo normal ba don scene din abinda ya faru jiya ya ki barin memory dinta da ya fado mata kuma sai gabanta yayi mugun faduwa, sai dai tana ganin motar daddy a parking space alamar ya dawo taji dadi har ranta. Tana fitowa wanka ta dau wayarta da ta boye a press ta bude, missed calls din Sadeeq taga ni har uku da text biyu bayan na jiya da daddare da bata bude ba, ta ki bude text din tayi lock din wayar ta mayar cikin press dinta ta gama shiryawa sannan ta fito parlor, Tana murmushi ta karasa ta gaida Daddy da ya fito parlor, daddy na kallonta yace "Lafiya lau Mamana, are you okay" ta buda ido tace "Sure daddy, ya hanya?" Yace "Alhmdllh, ya shirin walima" tayi yar dariya tace "Daddy Ina yi" Ammi dake jera ma Daddy abinci a dinning sae hararanta take, Daddy yace "Ga tsaraban ki can Ammin ki ta sa maki a fridge" cike da jin dadi tace "Toh nagode daddy" Da yammacin ranan Imaan ta tafi kai ma Inna abinci, sallama tayi ta shiga parlon, Daddy ne xaune parlon sae Kawu Bala, ga Umma ma xaune ta sha xumbulelen hijab kanta a kasa, ga wasu kawunnanta har biyu su ma a parlon, Inna dai na xaune kan tabarma tayi tagumi tana sharban kuka, ganin imaan ta shigo cikin rawar murya tace "Wllh bata fi wannan yarinyar muka aurota ba Talle" imaan ta gaishesu ta ajiye abincin hannunta ta fita. *Imaan isn't for free* it's 300 via Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah Then u show ur evidence of payment via my WhatsApp number 07087865788Daddy ne xaune parlon Inna bayan su kawu Bala, Umma da kawunnanta sun fita, Inna ta tace "Wlh wllh Bukar ka ji rantsuwar musulmi ko, to Rukayya ta ci albarkacin ka ne, don ina jin kunyan ka ainun, amma idan ta sake ko da min kallon banxa ne a gidan nan to aurenta da Ahmaduna ya kare ba ruwana, xan nuna mata ni na haifesa ba wani shegen ya haifa min shi ba, yanxu ma ni wllh darajar ka da na Mujaheed ta ci, tunda ni nayi wahala da shi kuma yana min biyayya, kai ma kuma kana min biyayya, matar da ma ba wai son matar ka take ba amma ka dinga tsayawa tsakanin ka da Allah kan lamuranta, ita bata ki ba ma ta cutar da Aisha ba wllh, kai kuma duk ka damu da lamarinta, duniya dai ba gaskiya" Shi dai daddy bai ce komai ba yana sauraranta, tabe baki tayi ta mike tace "Ni dai ba ruwana, kawai mata ta wani taho min da rubabbun mutane su ban hakuri, wllh ta ci albarkacin Mujaheed da sai na masu koran kare ba kunyar kowa xan ji ba, ba ruwana, matar da ba tsoron Allah gareta ba balle a raga mata" Daddy dai ya bi ta da kallo har ta shiga daki sai ga ta ta fito ta xauna tana kallonsa tace "Kana ji na Bukar, ni dai duniyar nan kaf ba wanda bai san imaan takwarata bace, kuma kowa yasan ita kenan Allah ya baka, ita kenan jikata a wajen ka, Toh ya dai fi babu ai, sabili da haka gaskiya ni dai ga dubu ashirin dina da nake ta tarawa a samo tikeken rago da ya kusa d'an mariki a yanka mata na saukan nan, Allah kuma yasa na tsoron Allah xata yi, yayi mata albarka ya hada ta da mijinta na gari wato wannan yaro Bulasawa...." Shiru Daddy yayi yana kallon kudin da take mika masa, tace "Haba ka amsa mana yaro, ka bar min hannu a sagale" d'an murmushi yayi yace "Amma Inna kin fa san ba ita kadai xata yi sauka a gidan nan ba" tace "Toh ai shi sa nace takwarata" ya girgixa kai yace "Ai Ummi ma takwarar ki ce" Bude Baki tace "Yau naga abinda ya isheni, ji Bukar da wani xance, to cewa nayi ban sani ba, ai xuciya ma na son mai kyautata masa, Ummi ko gaisuwar kirki tana min a gidan nan balle in dinga tuna cewa takwarata ce, ni dai ba ruwana a dinga jin tsoron Allah, yanxu meye ma'anar hakan da kafada salon Ahmadu ya ji ya kullace ni, ni dai gashi ka tafi bakin ka a leko ka siyo mata tikeken ragon da nace a kawo mata" mikewa Daddy yyi yace "Toh Allah ya saka da alkhairi, sai anjima" tace "Toh kai dai ka ja bakin ka kayi shiru, abinda naman ma duk xa a tsakura ma kowa da kowa a gidan" shi dai daddy bai ce komai ba har ya fita. Washegari asabar da wuri aka tashi a gidan aka fara girke girke, Ammi da Aunty ne ke girkin a nan bayan kitchen din su Aunty, abinci kala uku xa suyi, sae soye soye, tun daren jiya dama Ammi tayi samosa da spring rolls, Aunty kuma tayi cakes da doughnuts, Umma sai kai wa da kawowa take kamar dai me neman abu fuska a daure, ta shiga ta fita, babu dai wanda ta ce ma sannu da aiki cikinsu, su ma babu wanda ya kalleta, Maimoon ne da Ummi suka shigo kitchen ko wanne sanye da Sabbin dinkin da Daddy yayi masu na atamfa gaba daya su uku masu saukan har da imaan, da Hijab dinsu ash colour yana jan kasa, sosai suka yi kyau, Aunty tace "kun yi kyau sosai, amma kuna kallon agogo dai koh" Ammi tace "Allah ya sa ita wancan ta gama shiryawan" Maimoon tace "Shayi kawai xa mu sha sai mu je mu kirata" Muryar Umma suka ji bakin kofar kitchen din tana kallon Ummi cike da masifa tace "Kin wuce kin cire kayan nan na jikin ki ga lace can na dinka maki ko sai na 6ata maki rai???" Ummi ta kalli atamfar jikinta sannan tace "Lace umma?" Xagi umma ta kunduma mata tace "Don uwarki xo ki fita ki cire kayan nan, ko ubanki ne yayi maki" Ummi ta nufi kofa ta fita, Ammi dai sai aikinta take, Aunty ta tabe baki ita ma ta ci gaba da aikinta, tsaki Umma ta ja ta bar bakin kofar kitchen din, Maimoon ta hada masu shayin cup biyu ta fita, karfe bakwai da kusan rabi Imaan ta taho part din su Maimoon sanye da nata atamfar da well ironed hijab dinta har kasa, sosai tayi kyau Aunty tace "Iyye daughter tayi kyau sosai, amma ko yar powder baxa ki shafa ba Imaan" Yar dariya Imaan tayi ta gaida Aunty, Aunty ta amsa tace "Ki tafi daki ki dau powder Maimoon ki shafa kin ji?" Tana murmushi ta juya ta fita ta wuce sama, dakin su Maimoon ta shiga ta dau powder dinta dake gaban mirror ta shafa, ta goga chappete a lips dinta mai two colour, sosai tayi wani sanyayyen kyau kamar warce tayi wani kwalliya, juyawa tayi ta fita dai dai fitowar Umma dakinta, Sosai gaban Imaan ya fadi ta sunkuyar da kai har xata wuce maganan Sadeeq ya fado mata, a hankali tace "Ina kwana" Umma na mata shegen kallo tace "Kin sa6a gaisheni a gidan nan ne ko kuma gulma da kinibibi irin na uwar ki, to ko da mistake kika sake gaisheni a gidan nan wllh sai na gaura maki mari munafuka kawai sauran ciwo" Ita dai Imaan bata ce komai ba ta dinga sauka stairs, Umma ta bi ta da kallon tsana karara, har wani tafarfasa xuciyarta yake... Imaan na komawa kitchen Aunty tace "Ba gashi kin kara kyau abin ki ba, don kana da kyau kuma baxa ka kara da wanka ba" Imaan dai murmushi kawai tayi, Aunty tace "Kin dai karya koh?" gyada mata kai tayi, Aunty tace "Toh maxa ki tafi suna jiran ki a mota, sai mun xo in sha Allah" Imaan har ta nufi kofa ta juyo ta marairaice tace "Aunty xa ku taho da Inna?" Aunty ta d'an yi dariya tace "Tabb, to ban dai sani ba, amma kila mu taho tare" Ammi dai sai kallonta take ganin yanda ta rame kamar warce tayi ciwo na sati daya, Imaan tayi masu sallama ta fita kitchen din, ta tadda su Maimoon har sun shiga mota suna jiranta, ita ma ta shiga motar aka wuce da su islamiyyar su, Imaan dai sai Muraja'ah take a xuciyarta har suka iso islamiyyar tasu, Da yake islamiyyar sananne ne, kuma duk yawanci yaran masu shi sosai ne a makarantar, manya manyan mutane ba na wasa ba ne suka halacci taron waliman saukan, ciki kuwa har da 'yan gidan Bulasawa gaba daya, da shi kan sa Bulasawan, duk da yaran second wife dinsa kadai ke xuwa islamiyyar wato su Mariya da kanninta banda kannin Sadeeq don su tasu islamiyyar daban, amma hakan bai hana Mahaifiyar Sadeeq xuwa wajen saukan al-qur'anin ba, su Daddy da Abba da kawu Bala da Kanin Inna Audu d'an tsut kamar yanda ta kirasa duk sun xo gun saukan su ma, Sai da dalibai uku suka yi karatu sannan su Aunty da Ammi suka iso wajen, Imaan ta ji dadin ganin Amminta don ita ce seventh xata yi karatu Mariya kuma ta shidda, Maimoon ta goma, Tunda Imaan ta hada ido da Sadeeq dake wajen tare da mahaifinsa gabanta ya fadi bata sake yarda ta kalli direction din da suke ba, lkci daya duk mood dinta gaba daya ya canxa har aka xo kanta a karatun... And Sadeeq couldn't take his eyes off her even for a second, both her tajweed and kira'ah were more than perfect, babu wanda bai mayar da hankali kan karatun da imaan take na Surah Ad-dukhan ba.... Soo maa sha Allah, ta kuma burge kowa na wajen, first 20 Aya ta karanta na suran, Nan take kuma Bulasawa ya rubuta Check na 500 thousand ya mika ma Sadeeq dake kusa da shi yace "For her, she recited very well" Sadeeq ya amsa yana kallon mahaifin nasa, ba Bulasawa kadai ba, mutane biyu a wajen sai da suka ma Imaan kyauta, domin suran da ta karanta is perfectly talking about Islam, and those are who passed all their times playing, smoking, drinking, infact committing all such of sins, idan kuma Allah ya aiko da Dukhan daga sama su nemi gafara su tuba, daga ya dakatar su koma gidan jiya, Sadeeq ya mike ya je ya sami daya daga malamansu dake co-ordinating wajen ya mika masa check din yace "Daga Alhaji Ahmad Bulasawa xuwa ga dalibar ku Fatima Abubakar Imaan" Malamin ya amsa da jin dadi yana masa godiya yace "In sha Allah xai isa gareta" Mujaheed bai iso gun saukan ba sai karfe sha daya tare da Safeenah da ta cakare cikin tsadadden lace sai xuba kamshi take, Umma na ganinta ta dinga washe baki tana mata sannu da xuwa, ta mike daga kujerar da take xaune tace "Xauna ga kujerah Safeenah" Safeenah dake taunar cingam tace "A'a kiyi xaman ki Hajiya ga wani kujera can bari in je in xauna" Mikewa Umma tayi da sauri ta dauko mata kujeran tace "Gashi xauna" Safeenah ta ja kujerar duk da ido hudu da suka yi da Ammi da Aunty dake wajajen a xaune dauke kai tayi ta xauna tana kas kas da cingam, umma taji wani shegen dadi ganin abinda ta masu don sai murmushi take tace "In ji dai gidan lafiya Safeenah?" Safeenah na juya ido tace "Qlau wllh Hajiya" Da yake dalibai 20 ke saukan kafin karfe sha biyu da wani abu na rana duk suka gama karatun, A nan kuma malaman suka yi announcing kyaututtukan da Fatima Abubakar ta samu da wasu daga cikin daliban, tunda Imaan ta ji wai Bulasawa da kansa yayi mata kyautan kudi gabanta ya dinga faduwa, Umma dake wajen kuwa da taji amount din gaba daya hautsinewa cikinta yayi a wajen, ta kasa xaune waje daya sai mutsu mutsu take, Aunty kuwa sai murna take tana sa albarka, Mujaheed ya dinga kallon Imaan da ta ki yarda su hada ido da kowa, hotuna aka shiga yi a wajen, kowa hoto yake son yi da Bulasawa dake kokarin ganin ya bar wajen, Mariya ta ja Imaan daga wajensu Aunty tace "Come let snap with my family plss" haka Imaan ta dinga bin ta har suka isa inda familyn Bulasawan ke tsaye, Mariya ta ja ta xuwa gun Babanta tace "Abba xa mu yi hoto da ita, she is Fatima by name" Bulasawa na kallonta yyi murmushi yace "Maa sha Allah, keep it up Fatima" ta sunkuyar da kai tace "Nagode Abba" Photographer dake wajen ne ya dinga masu hoto, Sadeeq dake tsaye gefe yana kallonsu ya dawo gefen mahaifin nasa, Imaan na ganin haka ta fara kokarin sulalewa Mariya taki bari ta wuce har sai da aka masu hoton su hudu, gaba daya hankalin Umma na kansu kamar idanuwanta xa su fito, ko fasa auren Mujaheed da Safeenah da aka kusan yi kwanaki bai daga mata hankali kamar abinda ke faruwa yau ba, Wai Bulasawa da kansa yayi acknowledging Imaan, duk Aunty na lura da ita, Mujaheed dai na xaune shi ma sai kallonsu yake, Imaan suna gama hoto da Bulasawa ya bar wajen bayan ya bada donation dinsa na progress din islamiyyar, hotuna Imaan suka dinga yi da Mahaifiyar Mariya da kanninta, Mariya ta ja ta xuwa gun Mahaifiyar Sadeeq tace "Mummy xa mu yi hoto" Mahaifiyar Sadeeq na kallon Imaan da lovely smile tace "Ur recitation was sweet.. keep it up" Imaan na murmushi tace "Thanks Ma" Tsayawa imaan tayi kusa da ita aka fara daukansu hota tare da Mariya, Sadeeq dai bai daina kallon Imaan ba, har dai suka gama hoto da family dinsa ta tafi gun su Aunty, nan ma suka dinga hoto da su Abba da Daddy, Safeenah bata yarda ko da wasa suyi hoto da imaan ba haka ma Umma, duk suka ga Imaan na wajen basa shiga hoton, Imaan da Maimoon suka yi hoto da ya Yusuf da wasu daga frnds dinsa, shi dai Mujaheed na xaune yana danna wayarsa, Imaan na kallonsa ta isa kusa da shi ta durkusa a hankali tace "Yaya baxa mu yi hoto ba?" Daga kai yayi yana kallonta da manyan idanuwansa, ta turo baki ta kama hannunsa tace "Ni dai ka taso mu yi hoto plss" Ya d'an yi murmushi yace "To kira photographer din mu yi a nan" Tace "Noo, background din baxai yi kyau ba, ba ga flowers ba" Safeenah dake ta kallonsu ta karaso wajen kamar xata tashi sama ta xauna kujeran dake kusa da na shi har tana neman faduwa, Imaan na kallonta ta mike daga durkushen da take ta d'an tabe baki ta juya, Ba Safeenah kadai ba har Umma kallonsu take tayi mitsi mitsi da ido gashi ba daman yin komai ga Daddy da Abba a wajen, Mikewa Mujaheed yyi ya kamo hannun Imaan yace "Toh let go" Umma tayi still inda take ta bi su da kallo, gun flowers din suka nufa yana rike da hannunta, Mariya ya mika ma wayarsa duk da photographer dake kokarin daukansu yace "plss snap with my phone also" Imaan dai sai murmushi take, suna tsaye kusa da flowers din aka dinga kashe masu hoto kamar xata shige jikinsa, Mariya ma na daukansu da wayarsa Mujaheed couldn't help it but smiled sweetly, ta jinginar da kanta jikin shoulder dinsa tana murmushin ita ma, Safeenah ji tayi kamar xuciyarta ta fashe, ga wani tukuki da take ji a ranta, Umma dai sai murmushin karfin hali take tana gaisawa da jama'ah tana kallonsu ta gefen ido, Aunty dai na ta rarraba ma jama'ah abincin da snacks da suka kawo bayan sun ware na malamai da daliban saukan, Ammi kuma ta dinga raba buckets da books, Su kam familyn Bulasawa nan suka bar komai da suka kawo na sauka tun daga abinci, gifts, da dai sauransu suka yi wucewarsu, tashin hankali gun Sadeeq ganin har suka wuce imaan ta ki ko da kallon inda yake ba a cewa komai, tun da yake bai taba shiga tashin hankali na wannan lokacin ba tun daga jiya har xuwa yau, saukan ma banda Aunt dinsa ta tilasta sa da baxai xo ba, hatta Mahaifiyarsa sai da ta tambayesa damuwarsa gun saukan ganin gaba daya he is moody yace mata ba komai har dai suka bar makarantar bai ga fuskar tunkarar Imaan ba, ya dai je sun gaisa da su Abba da Daddy, sai su Aunty da Umma, sannan suka bar wajen da family dinsa, kafin azahar su Imaan suka bar islamiyyar a various cars xuwa gida, Tun da islamiyyar ta manya ce babu dalibi cikin masu saukan da ke da niyyar bin d'an uwansa dalibi gidansu kamar dai yanda ake yi yawanci, kowa kama gabansa yayi xuwa gidan iyayensa, ni ko nace ko dadi... Lol. Imaan da Maimoon motar Mujaheed suka shiga ta dalilin wayar Mujaheed din dake hannun Imaan don ita Mariya ta mika ma da xa su wuce, Safeenah ta wani hade rai xaune a gaban motar Mujaheed na driving har suka isa gida, yana gama parking Imaan na kallonsa a hankali tace "Yaya ka tuna promise da ka min few years back?" Ya juya ya kalleta, d'an murmushi yyi yace "Ban manta ba" tana murmushi ta sauka motar, Maimoon ta mika masa wayarsa ita ma ta sauka, Mujaheed xai sauka Safeenah ta rikosa fuska daure, juyawa yyi yana kallonta, tace "Ban ga fa'idar xuwan mu gidan nan ba bayan an gama sauka, I think it's better mu wuce gidan mu Doctor" Makullin motar ya jefa mata a cinya yace "Ki wuce gidan sai na xo, I don't think u have the right to tell me what to do and what not to do" daga haka ya rufe motar ya nufi part din su ta bi sa da kallo kamar idanuwanta xa su fito. *Imaan isn't for free* it's 300 via Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah Then u show ur evidence of payment via my WhatsApp number 07087865788Karfe biyu imaan ta fito daga bedroom dinta bayan tayi wanka ta canxa kaya xuwa daya daga sabbin kayan da Daddy yayi mata har kala biyar na waliman, sosai lace din ya amsheta, Ammi ta gama jera abinci kan lallausan carpet dake parlor, Tana kallonta tace "Ga abincin ku ke da Daddy" Imaan ta karasa ta xauna kan carpet din tana bude warmers din tana murmushi, Daddy ya fito daga daki ya karaso cikin parlon ya xauna saman lallausan carpet din shi ma yana kallonta yace "I am proud of you sweetheart" Dariya tayi tace "Daddy bayan ni ba ku ban gift ba kai da Ammi" yace "Let lunch first" Plate ta dauka ta xuba masu abincin da daddyn nata, Ammi dai na xaune parlon har suka gama cikin abincin, daddy na kallonta yace "Hope you will also pass ur up coming exams with flying colors by the grace of God" Imaan tace "Sure daddy" Daddy yace "Maa sha Allah" Makullin mota ya fiddo aljihunsa ya ajiye kusa da ita yace "And this is my gift" Imaan ya wara ido ta dau makullin tana kallo yace "A car?" Ammi dai sai kallonsu take, cike da jin dadi Imaan ta rungume Daddyn nata tace "I love you Daddy, Allah ya bar min kai, ya kara girma" Murmushi yayi yace "Ameen, gobe xa a taho da motar but you won't ride anytime soon, may be after ur waec" Imaan da ta rasa inda xata sa kanta sbda murna tace "Toh daddy, Allah ya kai mu, nagode Sweet dad, Allah ya saka maka da alkhairi" Yace "Ameen, clear this plates now" Mikewa tayi ta kwashe duk warmers da plate din ta kai kitchen, ta fito daga kitchen kenan aka danna bell, Mikewa Ammi tayi ta wuce dakinta, Imaan ta tafi ta bude Kofar, still tayi ganin Sadeeq tsaye hannunsa rike da leda, sosai gabanta ya fadi lkci daya ta juya da sauri ta bar bakin kofar Daddy na kallonta yace "Who's there?" Kasa basa amsa tayi ta wuce dakinta, bayan few seconds Sadeeq ya shigo parlon da sallama murya can kasa, Daddy na ganinsa yace "Welcome son" Sadeeq na kirkiran murmushi ya karasa ya ajiye ledan hannunsa ya xauna kasa shi ma ya gaida Daddy da ladabi, daddy ya amsa da fara'a yana tambayarsa ya mutan gidan, yace "Alhmdllh Daddy" Ammi ce ta fito daki sanye da hijab, ganinsa ta sunkuyar da kai tace "Sannun da xuwa" ya kalleta yace "Ina yini Ammi" tace "Lafiya lau, ya gidan?" Yace "Alhmdllh, fatan an watse taro lafiya" Ammi tace "Alhmdllh, mun gode Allah" dakin imaan ta nufa ta bude kofar ta shiga ciki, xaune ta ganta can karshen gado ta wani hade rai, Ammi tace "Wa kika ce ma Sadeeq xai xo gidan nan?" Kamar xata yi kuka tace "Ammi ni wllh ban sani ba kawai ganinsa nayi" Ammi tace "Toh sai ki tashi ki tafi ki kai masa ruwa da drinks ki dibar masa snack" Ammi bata jira cewarta ba ta fita dakin ta wuce nata, Mikewa Imaan tayi ta dau hijab dinta fari har kasa ta saka sannan ta fito, ta wuce kitchen ta hada ruwa da drinks sai glass cup a tray, ta debi snack a wani plate ta daura a kan tray din ta fito, kanta a kasa ta iso parlon ta duka gefensa ta ajiye, Mikewa Daddy yayi ya dau wayarsa yana kallon Sadeeq yace "Let me make a call outside" Sadeeq yace "Toh sai ka dawo daddy" daga haka daddy ya fita parlon, Imaan xata tashi ya rike hijab dinta cike da damuwa murya can kasa yace "Plss listen to me Imaan, don Allah ba don ni ba ki tsaya ki saurareni, am begging you plss...." Kasa cewa komai tayi ta xaune wajen ta hade kai da gwiwa ta fara kuka a hankali, duk ya rikice mata ya duka on his kneels yace "Don Allah kiyi hakuri ki yafe min Imaan, it's a mistake that will neva repeat itself again, don Allah ki min rai kiyi hakuri, I have neva for once had the intention of making you angry" ita dai ta ki cewa komai kuma ta ki dago kanta bata kuma fasa kukan da take a hankali ba, cikin sanyin murya yace "Kin ji Fatima, ki yafe min don Allah, wllh bani da nufin cutar da ke, I love you with every breathe of mine, I am wishing u to be the mother of my kids, ban taba ma ya mace irin son da nake maki ba, I Neva knew what true love is sai a kan ki, ni ba fasiki bane Imaan you can ask Mariya, sure I do flex with friends and I am a player, but i am very selective when it comes to mingling with girls, and mind you... ni ba maxinaci bane I can swear to you by Allah who made me ban taba ba, I am a type of person that find my opposite gender so irritating in every aspect, don't forget where I was born and raised, sure it's strongly against the teaching of our religion but kema kinsan to hug or kiss someone is part of our lifestyle back there, a haka na taso cikin su, I tried my very best getting rid of that while here in Nigeria kuma Alhmdllh there is improvement, wllh Imaan ban maki haka da niyyar in cuce ki ko in 6ata ki ba, mata ma dake kawo min kansu ban bata su ba sai ke da nake son aure? Kuma yanayin da nake shiga idan muna tare is something that I have neva experience all my life, that's why kika ga ko xuwa wajen ki bana son yi duk irin son ganin ki da nake I try my best staying away from u, plss Imaan kiyi hakuri ki yafe min, sharrin shaidan ne, don Allah ba don ni ba ki dago kanki ki kalleni in baki hakuri, na kuma maki alkawarin daga this very moment har xuwa ranan da Allah xai sa a daura mana aure idan ke matata ce baxan sake xuwa gidan ku ba, baxa kuma inyi requesting mu hadu ba, xa dae mu dinga waya kawai...." sai a sannan ta dago kanta hawaye na xuba idonta, lkci daya idonsa ya kada shi ma cikin sanyin murya yace "Don Allah kiyi hakuri Imaan" a hankali tana goge idonta tace "Na ji?" Kamar xai mata kuka har lkcn yana durkushe kan kneels dinsa yace "Kin hakura" a hankali ta gyada masa kai, yayi murmushin karfin hali yace "Toh nagode Imaan, Allah maki albarka" sunkuyar da kanta tayi, ya dauko ledan da ya shigo parlon da shi ya ajiye gabanta yace "This is for you, I am very proud of you today, Allah ya baki ikon amfani da karatun ki" ta kasa cewa komai, ya mike yace "Ki ce ma Ammi na wuce, thanks much for forgiving me" Bata iya tace masa komai ba ya nufi kofa ta bi sa da kallo, yana bude kofa kafin ya fita murya can kasa tace "Nagode" ya juya ya kalleta yayi murmushi sannan ya fita ya kulle kofar parlon, Bude ledan tayi taga tsadaddun turarruka ne a cikin ledan har kala biyar. Daren ranan Imaan na dawowa part din Inna ta je kai mata abinci suka hadu da Mujaheed xa shi gun Innar, Ya katse wayar da yake yi yana kallonta, ta wara ido tace "Yaya baka tafi ba?" Yace "Ehh wait for me a parking space yanxu xan fito" tace "Parking space?" Yace "Ehh" tace "Tohm" wucewa tayi shi kuma ya karasa part din Inna, Parking space din nasu ta tafi gun motarsa ta tsaya ta jingina jikin motar, Bayan kusan minti bakwai sai gashi, yana kallonta yace "I saw ur video... reciting, kinyi kokari kadan, they are still some corrections in ur tajweed, so ban ma san amfanin kyautar da aka dinga baki ba, may be dai Muryar ki ne yayi masu dadi" on a serious note ya kare maganar, xaro ido Imaan tayi tana kallonsa a sanyaye, lkci daya ta bata fuska ta sunkuyar da kanta, ko kallonta bai yi ba yace "Matsa in bude motata" a hankali ta matsa masa daga jikin motar ya bude, ta fara tafiya xata koma part dinsu, bin ta yyi da ido yyi saurin jawota, kuka ta fara yi a hankali, ya dawo kusa da ita yana murmushi yana kallonta gently yace "I was only joking Lil sis, ur recitation was superb, I love it, and that was what I expected" turo baki tayi tana kallonsa ya ja hancinta yana kallon eyeballs dinta murya can kasa yace "My future kids will have no problem with recitation of the holy Qur'an" Bai yi xaton xata ji abinda ya fada ba coz his voice was so low, as if he just murmured the sentence, ya ga ta xaro ido tace "Ehh?? Ur future kids that their mother is already hating me from day one" sai kuma tayi murmushi tace "Ba ruwana, idan dai sun xo gida xan dinga koya masu in sha Allah..." Yyi murmushin sa mai kyau yana shafa kansa yana kallonta, Jan hancinta yyi bai dai ce komai ba ya bude back seat ya fiddo Laptop sabo dalll, ya mika mata yace "My promise 3 years ago" wara ido tayi ta rungume sa tightly tace "Waow... Nagode yayana, I love ittt, you kept to ur promise" Mujaheed ya ji gaba daya kafafuwansa sun kasa daukansa ya jingina da motarsa ya lumshe ido and hold her closely to himself, Saketa Mujaheed yyi da sauri jin an bude kofar apartment dinsu, Imaan ma ta ja baya tana kallon direction din, Umma ce ta fito tare da Hajiya Saude xata rakata, imaan na ganinta dama ta bar wajen da sauri ta dau hanyar apartment dinsu, Umma ce ta fara hangota sai kuma ta fara kalle kallen parking space din don ganin ita da waye tana ganin Mujaheed ta bi bayan imaan da mugun sauri Hajiya Saude na biye da ita, fixgota Umma tayi tace "Uban me kike yi gun Mujaheed, me ya kawo ki wajen sa, meye wannan a hannun ki??" Umma ta kwace laptop din tana xaro ido tace "Meye wannan din ya baki?" Mujaheed dama na ganin haka ya taho gun su da sauri kafin imaan da ta wani 6ata fuska tana kallon umma tace komai yace "Noo Bata aka yi as gift na walima shine ta ke nuna min" Wani mugun kallo umma ta watsa masa tace "Take nuna maka kayi mata me, don tana karuwanci an bata laptop kuma sai ta taho nuna maka?" Da mamaki yake kallon Umma yace "Haba Umma, why all this" tsawa ta masa tace "Questioning dina kake yi? Sharri nayi mata ba iskancin take ba, ai wllh ko qur'ani xan iya dafawa in rantse iskanci take yi, ance maku a banxa yaron nan ke kashe mata kudi, ai kawai sai dai Allah ya shirya mana xuri'a, amma sai ta kawo wani shegen laptop ta nuna maka kayi uban me da shi??" Imaan dai kallon umma kawai take hawaye cike idonta, Hajiya Saude ta karbi laptop din tace "Lallai kam Allah ya shirya mana xuri'a amma dama waye bai san 'ya yan masu kudin nan ba" Mika ma imaan laptop din tayi tace "Karbi, Allah kuma ya shirye ki" Imaan taki amsar laptop din hawaye ya cika idonta, Umma tace "Sake mata tsiyarta mu wuce idan baxa ta amsa ba" daga haka umma ta wuce, Mujaheed ya sa hannu ya amshi laptop din hannun Hajiya Saude, ta bi bayan umma tana kyabe baki, Imaan ta fashe da kuka tana kallonsa, Bin uwar tasa yyi da kallo xuciyarsa na tafarfasa shi ma, har suka fita gate, kamo hannunta yayi ya wuce bayan apartment dinsu da ita suka tsaya cikin lallashi yace "Stop those tears imaan, she only said that to please her self, eraze her talk off ur mind now" shessheka ta fara yi, ya hade rai yace "Baxa ki daina kukan ba" goge idonta ta fara yi, ya sa hannunsa yana share mata idanuwan nata, murmushi yyi murya can kasa yace "You are taking ur pride to it rightful place in sha Allah Lil sis" turo baki tayi, sai ta basa dariya ya ja hancinta a hankali yace "My pretty stubborn Lil sis" ta sunkuyar da kanta bata ce komai ba, Mika mata laptop din yyi ta amsa yace "Yi wucewar ki ciki, on Sunday sai ku xo gidana tare da Inna in baki sauran gift din ki" make kafada tayi tana turo baki, yace "Why??" Ta wani hade rai tace "I dislike ur wife, I don't know.... I just don't like her" kasa cewa komai yyi yana kallonta, can a hankali yace "But it's also ur home, gidana ai naki ne" tace "Toh ai ita bata san haka ba, ko baka gaya mata bane" Dariya sosai ta basa don sae da yyi, ta tabe baki tace "Ni dai bana sonta kwata kwata" ya sauke ajiyar xuciya yace "Toh ni xan xo in dauke ku da kai na" imaan tace "Toh, kasan me Sadeeq ya bani" shiru yyi yana kallonta, lkci daya mood dinsa ya canxa, can dai yace "Waye shi?" ta wara ido tace "Lahh baka san sa ba Yaya? Toh ai shikenan, sai da safe" daga haka ta wuce da sauri tana murmushi ya bi ta da ido. Har titi umma ta raka Hajiya Saude suna tafe suna hira, Hajiya Saude tace "Toh ke kin dage tana karuwanci ta ya kika san haka" Umma tayi dariya tace "Ni kuwa xan fi kowa sani, ae ki bari kawai in Allah ya yarda sai uwarta Aisha ta ji kunya, sai ta gwammace a juyarta ta dauwama bata rufe bakin mutane da sauran ciwo ba" Hajiya Saude tace "Toh Allah ubangiji ya tabbatar da hakan, amma fa kamar Familyn Bulasawan ma naga sonta suke" Umma da taji ranta ya wani baci tace "Toh ae baxa su so d'an su ya auri warce ya lalata a waje ba, kuma muna nan sai Imaan tayi ciki a waje ba a dakinta ba" dariya sosai Hajiya Saude ke ta yi, Umma ta ja tsaki tace "Baki san ni bane, wannan yaron shine ajalin ita da uwarta, ba sai wani rawan kai suke uban ya mata kyautar rabin miliyan ba" *Imaan isn't for free* it's 300 via Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah Then u show ur evidence of payment via my WhatsApp number 07087865788kMikewa Mujaheed yyi da sauri ya wuce sama, Safeenah ta wani tabe baki ta ki tashi sai ma kwanciyarta da tayi kan kujerar, Inna na kallon Imaan da ke tsaye tana kallonta tace "Lafiya kika fito ko basa nan ne?" A hankali Imaan tace "Nima ban sani ba" Inna ta kutsa kai ta shiga parlon tace "Ina kuma xa su ranan lahadi su bar kofa ba makulli kamar tababbu, ko dai baccin asaran suke..." Suna hada ido da Safeenah dake kwance Inna tace "A'a Safara'u, to tace min ba kowa, anya Imaan na da lafiya ma kuwa, Ina Mujaheed din?" Safeenah ta mike tana kirkiran murmushi tace "Sannu da xuwa Inna" Inna ta xauna tace "Yauwa sannu Safara'u, ana ta shan iska kenan, to ba kya sha ba gari duk xafi don ma dai akwai Ac, ai nima idan naji xafin yayi yawa dama daga ni sai yar shimi da xani nake xama na parlor, kar xafi yyi min illa..." Mujaheed ne ya dawo parlon sanye da jallabiya milk color kansa a kasa, Inna na kallonsa ta washe baki tace "Ina kwana Mujaheed" ya karaso ya xauna yana dube duben parlon yace "Ina kwana" tace "Lafiya lau, yau ba aikin kenan" Yace "Sai da yamma" tace "Toh ai jiki da jini, in gaya maka daga gidan ta Rasulu nake mun je mun yi sirrin mu shine nace bari in biyo mu gaisa kafin mu koma gida" magana take masa amma gaba daya hankalinsa na kan kofa, Inna tace "Sai kuma wannan yarinyar tace min baku nan, kai kaji walakanci..." Bata rufe baki ba kamar jira yake yace "Tana Ina??" Inna tace "Oho ni dai ba na shigo ba, dama tun da muka fito take min walakanci tana ganin mai adaidaita xai min rashin kirki ta gudu ta bar mu..." Mujaheed bai ce mata komai ba ya mike ya nufi kofa Safeenah ta bi sa da kallon gefen ido, Bai ga Imaan a waje ba ya karasa gate yana kallon mai gadi yace "Warce suka shigo yanxu da kaka ta fita ne?" Yace "Ehh ta fita" Mujaheed ya fita gate din, can ya hangota har ta kusa titi, ya fi minti daya tsaye yana kallonta kafin ya juya a hankali ya koma cikin gidan, Inna na kallonsa tace "Ta ki shigowa ne halan? Rabu da ita ban iya wahala ni dai ai ta aan hanya" Bai ce mata komai ba ya wuce sama Safeenah da ta wani daure fuska ta bi sa da wani kallo. Bayan kusan minti talatin Mujaheed ya sakko downstairs sanye cikin kananun kaya hannunsa rike da makullin mota, Inna na xauna ga plate din farfesun kaji gabanta tana ta yaga tana ma Safeenah hira, Safeenah dai na xaune sai kallonta take uninterested, Inna na kallon Mujaheed tace "Ina kuma xa ka?" Yace "Ba dadewa xan yi ba...." Daga haka ya fita parlon, da sauri Safeenah ta mike ta dau Hijab ta bi bayansa, Inna na cewa "Maxa je ki ku yi sallama" Har ya shiga mota Safeenah ta samesa cike da shagwaba tace "Ina kuma xuwa sweetheart, bayan ka min alkawarin baxa ka fita ba yau" Ya tada motar ba tare da ya kalleta ba yace "Ba jimawa xan yi ba" Tace "Ohk then, bari in raka ka" sai a sannan ya kalleta yace "I don't think it's necessary Safeenah" da wani expression take kallonsa, yace "Forget about the previous plan on what to cook, tunda grandma na nan kiyi tuwo kawai with vegetable soup, I will be back soon" tana masa wani kallo bluntly tace "Wllh baxan yi ba, sai ka taho da tuwon daga inda xaka yanxu..." shi dai ba kulata ba ya rufe motarsa ya gama warming mota ya danna horn mai gadi ya bude masa ya fita. Mujaheed na isa gida yyi parking a waje, ya shiga compound dinsu, tun da ya shiga yake kallon part din su Imaan, gently yake tafiya, ya kalli apartment dinsu sannan ya wuce, yana isa part din su Imaan ya danna bell, sai kuma ya bude kofar yyi sallama ya shiga, Ammi ta leko daga kitchen taga ko wanene, gaisheta yyi ta amsa tana welcoming dinsa ta fito, Bai xauna ba yace "Dama kawai na shigo mu gaisa ne" tace "Toh nagode, ya gida?" Yace "Alhmdllh" tace "Maa sha Allah" ba tare da ya kalleta ba yace "Imaan na ciki ne?" Tace "A'a" da sauri ya juya yana kallonta, tace "Yanxu na aiketa taje kai ma Aunty sako" Bai san lkcn da ya sauke ajiyar xuciya ba yace "Toh, sai anjima" tace "Allah ya bamu alkhairi" fita yyi parlon ya wuce part din su, Umma na xaune parlor da Rahma suna magana kasa kasa, Umma na kallonsa da murmushi tace "A'a sannu da xuwa Mujaheed, yanxu ko nake cewa bari driver ya dawo xa mu je can gidan Hajiya Balaraba daga nan sai mu biya naka, tunda ku ka tare ban je ba" ya xauna ya gaisheta ta amsa tace "Toh ina Safeenar?" Ya mike yace "Tana gida tace a gaishe ku" Umma ta bi sa da kallo ganin sama xai wuce tace "Ina kuma xaka?" Yace "Xan dau wasu takardu a daki" Daga haka ya haura sama, murya can kasa Rahma tace "Ita fa Mariyan ma ba kowa take kulawa ba wllh Umma, bari dai Ummi ta dawo ki ji, ai ajinsu daya har schl" Umma tace "Toh ita Imaan din ta ta6a xuwa gidansu Mariyan ne?" Rahma tace "Suna xuwa da Maimoon sosai ma" Umma tace "Atoh, Da bata xuwa ai baxa su santa ba har su mata kyauta gun sauka, har fa da yin hoto da uwar yaron da kishiyarta" Rahma tace "Imaan da bata kula maza amma saboda taga d'an mai kudi ne she didn't think twice kafin ta fara kulasa, kila ma a gidan nasu suka hadu" Umma tayi wani murmushi, murya can kasa tace "Toh xa ki yi abinda nace maki din?" Rahma tace "Toh umma ai ba shiri muke da ita ba fa, gwara ma Ummi" Umma tace "Toh yanxu ai xata dawo..." Dakin Aunty Mujaheed ya bude yana kallon ciki, Maimoon ce xauna kasa kusa da Aunty dake xaune kan stool tana mata kitso, Imaan kuma na xaune kasan rug tana kallonsu, Imaan na ganinsa tayi saurin dauke kai, ya shiga ya rufe kofa idonsa a kanta, Maimoon ta gaishesa ya amsa, Aunty ta sake kitson da take tace "Welcome son" Mikewa Imaan tayi tace "Toh Aunty ni xan wuce" Aunty tace "Au kin fasa kitson kenan, dama nasan baxa ki yi ba, kice ma Ammi xan shigo nan da anjima" Imaan dake murmushi don ita kanta tasan kawai dai tace Aunty ta mata kitson ne amma ba yi xata yi ba, lokaci daya murmushin fuskarta yyi fading ganin Mujaheed ya fita dakin, tana ganin haka ta hade rai ta koma ta xauna tace "Toh tunda xa ki je shikenan, sai mu koma tare" Aunty tace "Toh shkkn" Mujaheed ya fi minti biyu tsaye corridor ganin bata fito ba ya bude kofar dakin, Aunty tace "Yau dai yan miskilancin na kusa ne ko doctor, Ina yini toh?" D'an murmushi yyi yace "Ina kwana Aunty?" Tace "Atoh, ka shigo Ina welcoming dinka kayi kamar baka ji ba kuma ka fita" ya shafa kai a hankali yace "An kira ni ne a waya na fita" Aunty tace "Ohk, ya amarya?" Yace "Tana gaishe ku" Aunty tace "Toh muna amsawa" duk irin yanda ya kafe imaan da ido bata yarda ta kalli direction dinsa ba, har ya juya ya fita, Imaan bata bar part din Aunty ba sai da ta gama ma Maimoon kitso suka koma part din su tare da Auntyn, har sannan kuma Mujaheed na xaune parlor, ya bi su da ido har suka fita Imaan ta saci kallonsa suka hada ido da sauri ta dauke kai ta shige gaban Aunty tana turo baki. Daren ranan Imaan na part din Inna suna dakinta, Inna sai famar rura wutan dake kasko take da baki, Imaan kuma na tsaye kamar xata yi kuka, Inna ta ajiye wutan tace "Ke dai ki daina haka imaan, ni wllh idan kina bani wahala xan tattara lamarin ki in xubar a kwandon shara, ya xa ki dinga ban wahala ina taimakon ki? Baxa ki cire kayan ba ki xo ki durkusa, kai wllh Bukar dai ya haifi jaraba" Imaan tace "Toh wai ni kin manta bana son hayaki ne, yanxu idan asthma dina ya tashi fa?" Inna tace "Meye kuma asma? Kiyi ta kira ma kanki ciwo, Ke dai ki ji tsoron Allah, abinda nace d'an minini xan yarfa a wutan ki shaka ko kadan ne sai ki fita da gudu, idan fa aka kashe ki ko digon hawaye na baxan yi asara ba wllh" Imaan ta rungume hannu tace "Wllh bana so ni dai, gwara inyi wanka da shi, haka kawai inje asthma na ya tashi inyi ta wahala" Inna tayi tagumi tace "Kai ina shan wahala ni patuu, ni dai ba don ki kadai Allah ya halitto ni ba wllh" tana fadin haka ta mike ta dau kullin magani ta wuce bayi tana cewa "Sai ki cire kayan, idan ya kama ma in cuda maki maganin da kai na sai in cuda maki baxan yi asaran kudi ne a banxa ba" Imaan na turo baki ta fara cire rigar jikinta, tana cikin cire skirt taji an bude kofar dakin, xaro ido tayi ta fasa ihu ta durkusa a kasa, da gudu Inna ta fito tana cewa "Shikenan ta fada cikin garwashi ta kai ni ta 6aro gun Bukar...." Inna ta gwalo ido ta kalleta ta kalli garwashin wutar don ta tabbatar bata fada ciki ba, Inna na nunata tace "Anya imaan xaki wanye lafiya da duniya kuwa??" Imaan da ta takure gu daya tace "Ni dai Inna wllh kice masa ya fita" da sauri Inna ta kalli kofa ganin Mujaheed tsaye ta xaro ido tace "Me xan gani haka?? Kai ya haka xaka afko mana daki ba sallama, baka ganta a tu6e bane Mujaheed, yaushe ka xama haka?" Shi dai bai ce mata komai ba ya juya ya fita, Inna ta tafe hannu tace "Yau naga abinda ya isheni, toh tsaye ya gan ki da ya shigo?" Kamar xata yi kuka ta gyada masa kai, Inna tace "Toh shi ya ga duhu wllh, tashi ki shiga kiyi wankan ki, shi yaga duhu" Imaan ta mike ta dau towel ta daura tana turo baki ta wuce bathroom, Inna tace "Kaji min gantalalle, Toh wani salon iskanci ne wannan xai shigo maki daki kin tu6e?? Ni dai ba ruwana, don mutum yyi aure kuma sai ya fiddo da fi'ilin iskanci iri iri, Toh wllh shi ya ga duhu" Tana fadin haka ta sa makulli a kofar tace "Ba ruwana" Tun daga wannan rana da imaan ta ga Mujaheed xata canxa hanya ta wani daure fuska..... Inna na parlor ta daura kafa daya kan daya da yamma tana kallon wani film Ummi ma na parlon ta gama mata kitso kenan, Inna sai tsine ma boss din film din da suke kallo take, duk ta cika parlon da muryarta, Ummi sai dariya take tana cin soyayyen nama da Inna ta yarfa mata a plate, sallama aka yi bakin kofa Inna ta amsa tana kallon kofar, Sadeeq ne ya shigo da leda a hannunsa, Inna ta mike da sauri tace "A'ahh sannu da xuwa Bukar, kai ne da yamma haka, Bisimillah" ya karaso yana murmushi ya xauna, Inna tace "Ya iyayen naka?" Ya xauna yace "Alhmdllh, suna gaishe ku" Inna tace "Tohh ina amsawa wllh, Ummi tashi ki debo masa ruwa a fridge da lemo, idan kuma baxa ki ba in tashi" Ummi dake kallonsa ta gefen ido ta mike ta nufi kitchen, ba a dau lkci ba ta dawo ta ajiye masa tray din drink da ruwa ya kalleta yace "Nagode" Ummi ta koma ta xauna tana kallonsa, Inna na kallon Ummi tace "Toh kiyi wucewar ki ai mun gama kitson ko? Allah maki albarka" Ummi ta wani hade rai sai kuma ta mike ta nufi kofa, ko ba a gaya ma Sadeeq ba yasan kanwar Mujaheed ce don kamar da suke ba na wasa bane, Inna ta tabe baki bayan ta fita tace "Toh sai ta wani xauna cikin manya, ai bai dace ba" Sadeeq na shafa kai yana murmushi yace "Dama Ina son xa mu yi magana ne Kaka" Inna ta gyara xama tace "Toh Bismillah, Ina jin ka Bukar in ji dai lafiya" Yace "Lafiya lau, dama Kaka Abbana ne ke min maganar aure tun da dadewa, na gaya masa yanda muka yi da ku a nan yana ganin kamar kawai xance nake masa...." Inna ta katse sa tace "Aa ba xance kake masa ba wllh su Ahmadu ne suka dakatar da kai, toh amma ni dama faduwa ta xo dai dai da xama, ba ruwana yau xan kira Ahmadun a gama magana, in sha Allah xuwa nan da Juma'ah ko lahadi xai ce ka turo magabatan ka, kwantar da hankalin ka Bukar in Allah ya yarda komai ya xo karshe, Sakandari?? An dade ba ayi sa ba in har xancen sakandarin xa su kara min, ni ba karamin aikina bane in tura ku kano gidan kawu Salisu ku kai gaisuwan da sadaki can" ya d'an yi murmushi, tace "Allah ba batun dariya ba, ai idan muka ci gaba da biye su Ahmadu da Bukar sai mu yi sa6o mu hallaka, haka kawai su ja mana fushin ubangiji kiri kiri suna fiffita abun duniya kan sunnar ma'aiki" a hankali Sadeeq yace "Toh nagode Kaka Allah ya kara girma" Inna tace "Atohh, duk ya ake ciki xuwa gobe xan kira ka kaji" Yace "Toh xan koma kaka" tace "Toh Allah maka albarka" ya ajiye mata ledan hannunsa yace "Ga turare na kawo maki Kaka" Inna tace "Kamar kasan bbu komai dakina sai fankon gwangwanayen turaren na jera gaban madubi" Yar dariya yyi ya nufi kofa ya bude, da sauri Ummi ta ja baya, sai kuma ta fara tafiya ko takalmi bata tsaya sa wa ba, Sadeeq ya bi ta da kallon mamaki bai dai ce komai ba ya fita ya sa takalmansa ya wuce, A gate ya kusa cin karo da Imaan xata shigo compound din hannunta rike da pack din bottle water, ta koma baya da sauri, ya wara ido ya fito murya can kasa yace "Baby" Ta sunkuyar da kai tace "Ina yini?" yace "Lafiya lau, where are u coming from?" Tace "Na je siyo ruwana ne" yace "Iyye bottle water kike sha kenan" murmushi tayi bata ce komai ba, yace "Toh kawo in taya ki kai wa ciki" ta girgixa kai da sauri tace "A'a nagode" Bata fuska yyi yace "Plss let me help" Bai jira cewarta ba ya kai hannu xai amshi ruwan, hannunsa na ta6a nata ta sake ruwan ba shiri, shima kuma da sauri ya janye hannunsa ruwan ya fadi kasa, dukawa yyi ya dauka yace "Ohh Subhanallah, sorry plss" Murmushin karfin hali tayi ta shiga gidan ya bi bayanta, Xaune Imaan taga Umma da Ummi kan fararen kujera a can Balcony dinsu Umma ta bata attention gaba daya, Imaan ta dauke kai da sauri, shima Sadeeq hakan yyi har suka isa part din su Imaan, imaan na kallonsa tace "When did you come?" Yace "Some minutes ago, am tired Imaan na xo na sami grandma ne plss a ban ixinin in turo magabatana ko ba yanxu xa ayi biki ba..." ita dai Imaan bata ce komai ba, ya ajiye ruwan hannunsa a kasa, ta duka ta dauka tace "Toh nagode sai mun yi waya" daga haka ta wuce ciki, ya bi ta da kallo sannan ya wuce yana murmushi. Abba ne xaune parlon Inna tare da Mujaheed da xuwansa gidan kenan, har Inna ta kai aya a xancen da take Mujaheed sai kallonta kawai yake, Abba dai kansa na kasa, can Abba ya daga kai ya kalleta bayan tayi shiru yace "Toh ai jarabawan ma saura wata daya da sati biyu in sha Allah Inna" Inna tace "Ku kuka jiyo wannan kuma ni ina ruwana, ya xa ku dinga maida ni karamar mutum gaban yaron nan, gaskiya wannan karan bana son magana da yawa sabili da kar raina ya baci, ga abinda nace in dai kuna tsoron Ubangijin ku, meye kuma wata daya da rabi Ahmadu? Shi auren ake gudu kuma yanxu ana rirrike boko hannu biyu, Me yasa ku ke haka?? Ni dai idan na isa da ku gwara a hada bikin ma da na wannan yaron Isuhu tunda an ma kusa kai sadakinsa" Mujaheed dake kallonta har sannan yace "Don dai an jira wata daya da kwanaki ban ga wani damuwa ba, hanxarin me yake??" Inna tace "Amma gaskiya idan xan yi maganar arxiki Mujaheed ya daina shigo min parlona, a daina xuwa min da shi" wani kallo Mujaheed ya dinga mata, tana kallon Abba da karfi tace "d'an bakin ciki ne fa Ahmadu, ya xai yi aurensa yaje can yana morewa da figaggiyar matar sa amma ya dinga yi ma yar Uwarsa bakin ciki, haka yake so tayi ta xama a gida kamar ba mashinshini?" Mikewa Abba yayi yace "Toh shkkn, xa mu ba yaron ranan da xai turo magabatan nasa in sha Allah" a fusace Inna tace "Yaushe?" Abba yace "Nan da ko kwana uku in Allah ya yarda sai a hada bikin da Yusuf yanda kika ce" Inna tayi murmushi tace "Toh Allah ya kai mu lafiya ya maku albarka" kallon Abba da ya nufi kofa kawai Mujaheed yake har ya fita yana amsa maganar Inna da Ameen, can ya kalli inna da ta mike ta fara kakkabe kujeru, yace "Kin kagu ta bar gidan kenan??" A fusace tace "Ba ruwan ka, wai ma dai meye hadina da kai Mujaheed??? Ni dai nasan na haifi Ahmadu amma wllh da babu abinda ya hada mu gwara kayi ta kanka, kiri kiri ka dinga nuna ma jikata bakin ciki??" Yana murmushi ya mike yace "In sha Allahu wannan auren da kike ta 6arin jiki a kansa baxa ayi ba, kuma har tsayuwar dare sai na yi akan hakan" salati Inna ta saki tana kallonsa, sai kuma ta fashe da kuka tace "Baxa ayi ba?? Ehh lallai ka zama dan iska Muhammad, ita yar Bukar kake ma bakin ciki?? Me ta maka xaka mata wannan fatan" ko sauraranta bai tsaya yyi ba ya fice daga parlon, a hankali yake tafiya don shi kansa bai ma san lkcn da ya fada mata hakan ba. Abba na komawa dama ya kira Daddy ya gaya masa yanda suka yi da Inna, Daddy dai bai iya yace komai ba, Abba yace "So yanxu na yanke ranan Sunday as ranan da xa ace ya turo parent din nasa, kai kuma sai ka dawo Saturday or Friday" Daddy ya sauke ajiyar xuciya yace "Toh shkkn Allah ya kai mu, Allah yasa hakan ne mafi alkhairi" Abba yace "Ameen" daga haka suka yi sallama ya katse wayar. Washegari Abba ya kira Sadeeq ya kuma basa izinin turo magabatan sa ranan lahadi, Sadeeq was so happy, farin cikin da bai taba yin irinsa ba duk tsawon rayuwarsa ya dinga yi ma Abba godiya kamar ya masa albishir da aljanna, Mujaheed dai na xaune parlon shi ma don tun safe Abba ya kirasa, amma banda danna wayarsa babu abinda yake, lkci daya ya dago yana kallon Sadeeq suna hada ido ya dauke kai, ya mike ya kai wayarsa kunne yyi excusing kansa ya nufi kofa hakan yasa Abba ma ya bi sa da kallo kamar yanda Sadeeq yyi. *Imaan isn't for free* it's 300 via Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah Then u show ur evidence of payment via my WhatsApp number 07087865788Ranan lahadi kamar yanda Abba ya tsara hakan ce ta faru, don Mahaifan Sadeeq a ranan suka xo gidan nema masa auren Imaan, Bulasawa ne sai kanninsa biyu, da abokansa biyu, da kuma wani kawunsa suka taho gidan, shi dai daddy baya cewa komai don har ransa bai son aurar da only child din tasa a lkcn, a da ya dau burin sai ta kusa gama University amma yanxu gaba daya Inna ta gama ruguje plan din, kuma babu yanda ya iya, dubu dari biyar iyayen Sadeeq suka bayar kudin gaisuwan da akwatuna har guda takwas da sauran abubuwan da ake badawa a al'adance amma triple triple suka kawo komai, sannan suka ajiye ranan da xa su dawo a saka rana, Umma tunda ta sami labarin shigowar su gidan ta kasa xaune waje daya ta dinga safa da marwa a daki, can dai ta kira Hajiya Balaraba duk ta sanar mata abinda ake ciki, Hajiya Balaraba tace "Toh meye abun daga hankali Hajiya Rukayya, ke fa an gama baki tabbacin babu auren nan, ba abu bane da xai taba yiwuwa, to meye abun damuwa kamar baki yarda da bawan Allahn nan ba...." Hankali tashe Umma tace "Nasani Hajiya Balaraba ba wai ban yarda bane, na ji fa har ynxu shiru shiru ba alamar komai, ko xuwa gidan ma wllh yaron ya daina, ita kuma yarinyar gaskiya bbu wani linkage tsakanin mu, bbu ta ynda xa a hadu har yau ban yi yanda aka ce min ba, ga lkcn na ta wucewa..." Hajiya Balaraba tace "Bata tahowa bangaren ku ne?" Umma tace "Sae ta yi wata ma bata shigo ba idan ba uwar bace ta aikota, shi ma iyakarta dakin Amina" Hajiya Balaraba tace "Ke dai baki da dubara wllh, ga dai wajen da take xuwa kullum wajen Hajiya Asabe, ke baxa ki hada wani dubaran ba daga can" Umma ta d'an yi shiru kafin tace "Toh shkkn xan duba, can din ma ni ba haduwa muke ba ko na je gaishe da tsohuwar, xa dai mu yi waya xa a shigo min daki...." katse wayar tayi da sauri jin an bude kofa, Aunty ta shigo da farin ciki sosai tace "Hajiya an kawo kudin gaisuwan Imaan dubu dari biyar, kayan na gani Ina so kuma akwatuna takwas daga gidan Alhaji Bulasawa...." Umma ta dauke kai ta mike ta fara kakkabe gadonta tace "Toh Allah dai yasa ba yaudara bane, mu dai namu ido, wani kudin auren kirki ne har dubu dari biyar ba ma sadaki ba kamar xa a siyar da ita" Juyawa Aunty tayi ta fita dakin, Su Bulasawa na barin gidan Abba ya sa su Ummi da Rahma da Maimoon su kwashi kayan su kai part din Inna, Inna ta saki baki tana kallonsu suna shigo da kayan tace "Meye haka kuma?? Meye wannan din" Maimoon na murmushi tace "Na Imaan" Inna ta mike da sauri tace "Wa ya kawo?" Maimoon tace "Daga gidan su Sadeeq" tuni Rahama da Ummi suka fice parlon xuwa dauko sauran, Inna ta saki wani kabbara sai kuma ta xaro ido tace "Yaushe suka xo?" Maimoon tace "Basu dade da tafiya ba" Xaunawa Inna tayi ta fashe da kuka tace "Allah sarki Bukar, ita kenan fa garesa, ita kenan Allah ya basa gashi yanxu xai raba sa da ita... Yanxu ya xai yi da ran sa" Shigowar Abba yasa tayi shiru tana share hawayen idonta, Abba ya xauna ya gaisheta, ta amsa cikin rawar murya tace "Yanxu shkkn raba Bukar xa ayi da Imaan ni patuu??" Abba dai bai bata amsa ba ya ajiye ledan hannunsa a kusa da ita yace "Kudin gaisuwar da suka bada kenan" Inna ta xaro ido tana kallon ledan kudin tace "Nawa?" Yace "Dubu dari biyar" Inna ta saki salati tace "Toh dama ku siya mata dankareren gwal ku ajiye kar a ta6a mata ko biyar tunda ba wani xai mata xaman auren ba Ahmadu" Abba dai bai ce mata komai ba ya mike yace "Xuwa anjima xa mu shigo da Abubakar" daga haka ya fita parlon, Inna na murmushi ta daga hannu sama da karfi tace "Alhmdllh, Alhmdllh, takwarata tayi goshi ni Asabe, Allah na gode maka Allah, Allah na gode maka, ka bar min rai da lafiyar kai ta dakinta da hannuna in sa mata albarka" sai kuma ta fashe da matsanancin kuka, Maimoon ta tabe baki ta ta fita xuwa debo wasu kayan. Bayan Magrib Inna na share parlonta don ba a dade da fitar Aunty da frnd dinta sai frnds din Ammi biyu ba sun shigo ganin kaya, Yusuf ne ya shigo parlon bai dai xauna ba yana kallon Inna daga tsayen da yake yace "Ina yini" ta mike ta ajiye tsintsiyar hannunta tace "Lafiya lau Isuhu, sannu da xuwa bari in bude maka kayan, wllh babban akwatin babu atamfar kasa da dubu hamsin, gaba daya Holland da England suka xuba mata, ba fa lefe ne kayan sun gani sun kyasa ne..." Xata fara sauke sauke yace "A'a ba sai kin bude ba, dama Allah ya sanya alkhairi na xo maki, Allah yasa ayi muna da rai da lafiya" Inna tace "Atohh, Ameen dai, dama ganin kaya ai sai mata, kuma ai rana daya xa ayi bikin da naka idan Allah ya yarda, kai ka angwance kanwar ka ita ma haka" shi dai bai ce mata komai ba ya nufi kofa yace "Sai anjima" tace "Mu jima da yawa, Allah maka albarka, Ina nan ina lissafin wa enda suka shigo yi ma jikata barka, har yan anguwar nan ina xuba ido in ga wa enda xa su shigo da wa enda baxa su shigo ba, mutane uku dai sun shigo daxu, amma kaga Rukayya da Aisha ko keyarsu ban gani ba kuma xan ji dalili gobe da safe, ita Imaan din ma ban ganta ba yau gaba daya" shi dai tuni ya fita. Inna na xaune tana cin abinci aka bude kofa, Mujaheed ne ya shigo parlon ta mike da sauri ta shige daki sai ga ta ta fito da katon bargo ta rufa ma akwatin har tana neman faduwa, shi dai kallonta kawai yake, ta tabbatar ko kalan akwatun ba a gani sannan ta koma ta xauna tana ci gaba da cin abincinta tace "Wa alaikumussalam" Yana tsaye yace "Ina yini" tace "Lafiya lau" Bai kuma ce mata komai ba ya juya fita parlon ta mike ta rufe kofar tace "Gaskiya xan kira Ahmadu ya ja ma mutumin nan kunne ya daina shigo min nan, yaje can ya ji da xabiyar matarsa, kwata kwata xuciyarsa ba shi da kyau, hassada bakin ciki duk sun taru sun masa yawa, hooo ni patuu Allah ya ba ma Ahmadu Ya ya, sai dai Allah ya raba mu da su lafiya" Imaan ta fito wanka kenan daure da towel taga wayarta na haske, ta tafi gaban mirror ta dauka tana kallon screen din, pick din kiran tayi ta kai kunne tana murmushi, shi yyi sallaman ta amsa a hankali, yace "Why ain't u picking sweetheart" ta wara ido tace "Ina parlor ban jima da shigowa ba" Yace "Ohk, ya gida?" Tace "Lafiya lau" yace "Kayan sun maki dear?" Ta d'an yi murmushi ta sunkuyar da kai kamar yana gabanta tace "Ai bn gani ba" da mamaki yace "Why?" Nan ma dai murmushi kawai tayi bata ce komai ba, murmushin shi ma yyi yace "Ina fa mancewa bafillatana xan aura, to ya xa ki yi da ni da kunyar ki Imaan" ta turo baki tace "Nima bn sani ba" Yar dariya yyi yace "Xa ki sani ne ma" ita dai bata ce komai ba, yace "I can't wait imaan, in gan ni tare da ke as married couple" tace "Uhm ina son in shirya, I just took my bath now" yace "You need a helping hand?" Ta xaro ido tace "Noo, sai anjima" Bata jira cewarsa ba ta katse wayar, d'an murmushi tayi ta fara goge jikinta. Umma ce xaune parlon gidan Mujaheed tare da Safeenah dake danna waya tana mata sannu da xuwa, bayan sun gaisa tace "A kawo maki ruwa Hajiya?" Umma tace "A'a Alhmdllh, ai daga gida nake, Mujaheed din na nan?" Tace "Yana gun aiki" Umma tace "Toh madallah, na xo don Allah xa mu yi wata magana da ke ne mai muhimmanci" Safeenah na kallonta tace "Toh ina ji Hajiya" Umma ta d'an yi shiru sai kuma tace "Wannan yarinyar da tayi sauka kwanaki Imaan na xuwa gidan ki kuwa?" Safeenah na yatsine fuska tace "Yauwa dama don Allah Ina son kawo maki wani kara Hajiya, kinga ni dai da Mujaheed xai aureni ba wai ance min cousins dinsa xa su dinga xuwa min without good reasons ba kuma ba tare da sanina ba, don haka, don Allah a dakatar da wannan yarinyar daga xuwa gidana bana so, kada Watarana abu ya 6aci, sannan wannan kakar tasa ita ma kusan kullum sai ta xo, don tare ma suke xuwa da cousin din tasa" Umma ta xaro ido tace "Haba dai, kice suna xuwa nan sosai" Safeenah ta tabe baki tace "Ai kam, ni dai na gaji, sannan idan Yarinyar ta xo tayi ta nuna min isa da gadara a gidana ko gaisheni fa bata yi" Umma tayi dariya tace "Toh ai a kanta ma na xo gidan nan yanxu haka, Kinga kenan faduwa ya xo dai dai da xama" Safeenah ta bude ido sosai tana kallonta tace "Toh Ina ji" Umma ta gyara xama tace "Kin san d'an gidan Bulasawa??" Safeenah ta d'an yi shiru sai kuma tace "Gaskiya a'a, ina dai following din yaransa mata a Twitter" Umma tace "Toh d'an sa na fari ne ke neman Imaan din da aure, jiya aka kawo gaisuwa dubu dari biyar, da akwatuna takwas da sauran tarakace me yawa, wllh da kinsan abinda uwar yarinyar nan ta min a rayuwar duniya da kin tausaya min ke ma ki taya ni bakin ciki da auren nan" Safeenah dake gwalo ido tace "D'an Bulasawa fa?? Me ya gani tare da ita yake sonta?" Umma tace "Toh wllh sauran ciwo ce ma, yau ciwo gobe lafiya tunda sickler ce" Safeenah na gyara xama tace "Tabb, Shi sa take ma mutane wani gani gani kenan???" Umma tace "Wllh don haka yanxu kawai so nake kada auren ya faru, ni dai ba shige shige nake ba balle ace, ba ruwana da boka ko malam, kawai dai da yan dubaru xa a raba su, kema kuma dole sai kin bada contribution" Safeenah tace "Toh ta yaya?" Umma tace "Ba kince tana xuwa gidan nan ba, dama nima naji labarin suna xuwa da kakar, shi yasa nace bari in xo in same ki" Safeenah tace "Ba dai ko da yaushe su ke xuwa ba sai jefi jefi" Umma tace "When last suka xo??" Safeenah tace "xai yi kusan wata daya, Umma tayi tagumi tana naxari, can ta kalli Safeenah da ita ma tayi shiru xuciyarta fal takaicin wanda Imaan xata aura, wai yaron Bulasawa, Umma tace "Kinsan me xai faru yanxu Safeenah" Safeenah ta kalleta tace "A'a" Umma tace "Ki jira sai Mujaheed din ya dawo sai ki ce masa kwana biyu baki ga Inna ba, yaushe xata xo?? Ko kuma kyalesa kawai bari in baki lambar Innar ki kirata sai bayan kun gaisa sai ki tambayeta kwana biyu shiru shiru baki ganta ba yaushe xata xo??" Safeenah tayi murmushi tace "Koh?" Umma tace "Ahaf jikinta na rawa xata xo, ai ita tana son a dinga nuna ana ji da ita, kuma in xata xo da wuya ta xo ita kadai, Dole da Imaan din take fita kinga shikenan Allah ya kawo mana ita har gida amma kar ki yarda ki gaya ma Mujaheed kamar yanda nace da farko don akwai sa da kwakwalwa, nan da nan xai gano ki" Safeenah tace "I thought as much, ga wayar ki sa min lambarta" Umma ta amsa wayarta ta saka mata lambar Inna daga nata wayar sannan ta mika mata, Safeenah ta amsa ta kai kunne, Inna na dagawa ta rafka sallama, Safeenah ta amsa tace "Ina yini Inna?" Inna tace "Lafiya lau, waye don Allah, ni dai aiki nake ta yi na bude ma mutane akwatuna tun safe suna shigowa gani, kinsan duniya ba gaskiya yanxu sai a samu rikakken barawo da xai boye abu ya wuce da shi shi sa nake sa ido" Safeenah tace "Safeenah ce Inna" Inna tace "Waye Safeenah kuma?" Safeenah ta tabe baki tace "Matar Mujaheed" Inna tace "Ayyo, Safara'u ce, Toh sannu kin ji labarin an kawo kaya kenan?" Safeenah tace "A'a ban ji ba" Inna tace "Atoh wa xai gaya maki dama d'a bakin ciki uwa bakin ciki, wllh har yanxu ban ga keyar Rukayya ba, Mujaheed kuwa tunda ya shigo ya gaggasa min magana ban kara ganinsa ba sai jiya da aka kawo kaya, bakina a leko na shiga daki da gudu na dau katon bargona na rufe ma yarinya kaya da shi tun bai kai ga gama kirga guda nawa bane, akwatuna takwas ne da kyar ake xuge xif din, Toh me xance banda in gode Allah, har da gwal na dankunne guda biyu da xobuna biyu fa a ciki, ni dai ba ruwana duk me ma jikata bakin ciki Allah shi yasan yanda xai yi da shi, ko ke wllh baki samu haka ba shi sa Mujaheed ya fito kiri kiri ya nuna bakin cikinsa a fili, kwana nayi Ina al-ajabin abinda ya gaya min ranan wllh, isuhu kuwa har nan ya xo ya min Allah sanya alkhairi...." Safeenah da Umma sai sauraronta suke don a hands free Safeenah ta sa wayar, Umma ta wani kankance ido tana kallon wayar, Safeenah ta tabe baki tace "Toh Allah ya kyauta, yaushe xa ki billo Inna kwana biyu shiru" Inna tace "In billo a yashe ma yarinya kaya in shiga uku Safara'u, ai ba xancen billowa sai na kai Imaan dakinta, sa ido yayi yawa gwara in mike tsaye kyamm, toh ke baxa ki xo ganin kayan bane kike jira in billo?" Safeenah ta kalli Umma, Umma ta gyada mata kai da sauri alamar tace xata xo, Safeenah ta tabe baki tace "Toh xan shigo in sha Allah" Inna tace "Atoh, sai kin xo, sai kiyi sauri don xuwa anjima xa a kai ma kakarta ta wajen uwa ta ga kayan ita ma, sannan a maido min inyi gadin kayana" Safeenah tace "Toh sai anjima sai na xo" Bata jira cewar Inna ba ta katse wayar tana kallon Umma da tayi tagumi, Safeenah ta ja tsaki tace "Ai nima sai inda karfina ya kare wajen ganin auren nan ya fasu wllh, wato shi sa yarinyar ke ganin kowa banxa, ita a dole xata auri yaron Bulasawa to taga samu ta ga rashi tunda har labari ya xo kunne na kuwa" Umma tace "Wllh da kin gama min komai a duniya idan har muka hadu muka tarwatsa lamarin nan, Kinga wahalar da na sha gun uwar yarinyar nan wllh kwakwalwarki baxai dauka ba, ta dalilin uwarta aka min kishiya, aka kuma sakeni...." Nan umma ta fara giggila ma Safeenah karya da gaskiyar abinda ya hadata da Ammi, tana kai wa aya, Safeenah ta gyada kai tace "Ki kwantar da hankalin ki Umma, ai tunda har labari ya xo kunnena an gama komai, dama kwata kwata na tsani yarinyar tun daga ranan da na fara daura ido kanta, ki manta da ko wani shiri da kike a da ki sa min ido" Umma tace "Atoh, shkkn.. Amma fa baxan mance shirin da nake ba, don kunya ba kadan ba nake son Uwar yarinyar ta kwasa a hannu, yanxu dai ki shirya anjima kije ganin kayan kada a dago komai a rai" Safeenah tace "A'a rashin xuwan kawai ya fi, ban gani ba balle raina ya kara 6aci" sai kusan yamma umma ta bar gidan ko digon ruwa bata sha ba, amma ko a jikinta. Yau tun safe Mujaheed ke xaune garden din gidansa har wajen sha biyu na safe, Safeenah ce ta shigo garden din cikin shiga ta alfarma tana taunar cingam tana kallonsa tace "Doctor d'an baccin weekend din ma gaba daya baka yi ba yau, ni dai yanxu fita xan yi, xan je can gida daga nan kuma in tafi gidan ku in gaida su umma" Daga kai yyi ya kalleta calmly yace "Baxa ki ba" Safeenah ta gwalo ido tace "Baxan je ba kuma, mahaifiyata da taka xan je gaidawa fa" ya mike a d'an tsawace yace "Nace baxa ki fita gidan nan ba Safeenah..." Daga haka ya wuce ya bar ta wajen tsaye, ta ja tsaki tace "Don kana fama da miskilancin ka kwana biyu sai ka sauke kai na, Toh wllh sai na fita" Kiran Umma tayi da wayarta ba a dau lkci ba Umma ta daga, ko gaisuwa babu Safeenah tace "Toh gashi dai ya ki bari na in fita wllh kuma yau ya kamata mu yi abinda ya kamata, kusan sati daya kenan Mujaheed magana da kyar yake min a gidan nan, ni ban damu ba don dama haka yake wani lkcn amma na wannan karan yyi yawa, tun asuba yake xaune garden yau wllh kamar maraya, during weekdays kuwa dama sai nayi bacci yake shigowa ya fice kuma da sassafe washegari, kwata kwata na rasa gane kansa ban san me ke damun sa ba, ni duk wannan ba wani damuna yyi ba don a sauki na, amma yanxu gaskiya ki kirasa ki masa magana don idan har ban fito ba yau shirye shiryen mu ya ruguje ne kawai" Umma tace "Kyaleni da shi kawai, mu ma nan ai ya fi satin bai xo ba, Ina ga halinsa na da ne ke kokarin dawowa" daga haka umma ta katse wayar, Safeenah ta tabe baki ta wuce cikin gidan, tana ta xaune parlor har bayan minti talatin ganin bai sakko ba ta mike ta wuce sama, ya fito wanka kenan ta shiga dakin, yana mata wani kallo yace "Kin xata kiran da kika sa mahaifiyata tayi min xai sa ko fita gidan nan ne yau??" Ta nufesa tace "Wai me ke damun ka two days ne Mujaheed, dubi fa you look so pale, and ni dai nasan lafiyar ka qlau" Ko kallonta bai yi ba ya bude press dinsa ta rungume sa ta baya tana shafa chest dinsa cike da shagwaba tace "Ni dai wllh ka gaya min meye damuwarka mijina" Bata jira cewarsa ba ta juyo da shi ta rungume sa gam tana shige masa and she really turn him on.... *Imaan isn't for free* it's 300 via Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah Then u show ur evidence of payment via my WhatsApp number 07087865788Safeenah na gama shirinta ta daura dankwali ya xauna dass a kanta ta feshe jikinta da turare, ta juya ta kalli Mujaheed dake kwance idonsa rufe, karasawa kusa da shi tayi ta xauna gefensa tana ta6a dogon hancinsa ta kai bakinta fuskarsa a hankali tace "Dear ni xan wuce fa" Bude ido yyi calmly yace "I said you are going no where Safeenah" ta xaro ido tana kallonsa da mamaki don duk tunaninta ya hakura, can ta marairaice tace "Haba dear, wllh fa ba dadewa..." Ya katse ta ya mike xaune fuska daure yace "Nace baxa ki fita ba, am telling you this wllh idan kika fita gidan nan yau xaki san wanene Mujaheed" Yana fadin haka ya mike ya shige bathroom, tagumi tayi xuciyarta na tafarfasa ta bi sa da ido, can ta mike ta fice daga dakin rai bace ta kira Umma tace "Toh wllh ya ki bari na in fita Hajiya, taurin kan Mujaheed har tsoro yake bani" da mamaki Umma tace "Ya ki barin ki kifito kuma??? To ina Ina xuwa..." daga haka Umma ta katse wayar, Ba a dau lkci ba ta sake kiranta tace "Toh ai wayar tasa a kashe yake" Safeenah tace "To ya kashe kenan..." Safeenah ta tabe baki, Umma tace "Toh ki kai masa wayar ta ki" Safeenah tace "A'a ni kam baxan iya kai masa ba, don he is very serious, ki bari dai in ta lallabasa anjima xan kira ki" daga haka ta katse wayar. Imaan na xaune dakinta sun gama waya da Sadeeq kenan ta shimfida darduma ta dau Al-quran dinta ta ajiye a kai ta xauna kan darduman ta tankwashe kafa ta bude qur'anin, ba karamin missing din islamiyya take ba yanxu, ji take da ma bata yi saukan ba, Bude kofar dakin aka yi Ammi ta shigo, Imaan ta daga kai tana kallonta, Ammi ta xauna gefen gadon tace "Karatun kike ko kin gama" Imaan tace "A'a ban fara ba" Ammi tace "Kin ma ci abinci kuwa" Imaan tace "Ehh na ci" Ammi tace "Ohk, kina ji na Imaan?" Imaan na kallon mahaifiyar tata tace "Ehh ina ji Ammi" Ammi tace "Pls Ina son ki dage da azkar sosai kuma a ko da yaushe, make that a part of you, kuma da daddare xan dinga shigowa ina tashinki kiyi sallah...." Da mamaki Imaan tace "Ammi me yasa" Ammi ta buda ido sosai tace "Me yasa, dama sai da dalili mutum xai rike addu'a da tsayuwar dare, ae yanxu ne kika lalace baki yi, amma da ai kina yi sosai" Murmushi Imaan tayi bata ce komai ba tana bude kur'anin gabanta a hankali, Ammi tace "Ga kuma jarabawar ku ya kusa shima sai ki dage da addu'an samun nasara kin ji" Imaan tace "In sha Allah Ammi" Ammi tace "Good" daga haka ta mike ta fita dakin, imaan ta fara karatun Qur'anin gabanta cikin cool voice dinta. Da magrib ta tafi kai ma Inna abincin Inna ta ki barinta ta tafi ta dinga sauke akwatuna tana bude mata tana cewa "Sai kace ba kayan ki ba yau kusan kwanan su biyar kin ki ganin abinda ke ciki, ni dai ba ruwana, karere ma da abun bai shafesu ba duk suna ta xuwa gani balle ke" xauna ni dai ki duba, su Ahmadu da Bukar ma duk sai da na fiddo masu suka gani filla filla, Imaan dai ta d'an yi murmushi ta xauna tana kallon kayan da Inna ke fiddowa amma bata ta6a ba, Inna tace "Ni dai naga abinda ya isheni, to ki daga mana ki dudduba ke fa babu abinda ya hadaki da fulanawa, ubanki bahaushe ne gaba da baya, uwar ki ce bafillatana sai uwarsu Mujaheed, ban san me yasa suka nace sai fulani ba, nima dai ubana bafillatani ne amma uwata bahaushiya ce, mijina kuma bahaushe" Imaan ta turo baki ta dinga daga kayan tana kallo, Inna tace "Wannan ai jaraba ne ke da kayan ki baxa ki duba ba, ga gwal din can na hada da dankunnen da ya ta6a baki, bari in dauko ki gani" Daga haka ta shige daki, Imaan na ganin haka ta mike cikin sanda ta nufi kofa ta fice parlon da gudu ta sa takalminta tayi gaba, a hanya ta kusa cin karo da Mujaheed, ta xaro ido ta juya masa baya da sauri xata bar wajen ya kamo hannunta ya juyo da ita, kin yarda su hada ido tayi tace "Ina yini" ya dawo da ita jikin bango ya dago kanta yana kallon kwayar idonta, kallonsa ita ma take, lkci daya ta sauke idonta kasa a hankali, Murya can kasa yace "Me yasa kike gudu idan kin gan ni Imaan" ta turo baki tace "Ni fa ba komai yaya" ya kamo hannunta yace "A'a ki gaya min pls, me yasa kike gudu" kasa cewa komai tayi, yace "Imaan" da sauri ta kallesa jin yanda ya kirata, yace "Talk to me plss" Boye fuskarta tayi tace "Ni bana son ka min fada shi sa nake gudu" yace "Fadan me?" Kin cewa komai tayi ta sunkuyar da kai tana murmushi, ya kara kiran sunanta, kamar xata yi kuka tace "Abinda nayi mana" Bai iya yace komai ba sai kallonta yake, Jin shirun yyi yawa ta daga kai ta kallesa suka hada ido, ta wara masa idonta tace "Amma dai baka da lafiya ne Yaya" Ya sauke idonsa kasa yace "Probably" cike da damuwa tace "What's wrong with you yaya?" Da kamar baxai ce komai ba sai kuma a hankali yace "Akwai wani abinda ke shirin faruwa that will cause me lot of harms a rayuwata, and sure that will be the end of my happiness..." Da damuwa sosai tace "Subhanallah, what's that Yaya? Meye shi ka gaya min" jingina yyi da bango bai iya yace mata komai ba, ta dawo tana facing dinsa ta kamo hannunsa kamar xata yi kuka tace "Yaya don Allah ka gaya min meye shi, meye xai faru and how are you to prevent it from happening" Taku da suka ji toward direction dinsu yasa tayi saurin sake masa hannu bayan sun yi ido hudu da Abba dake tahowa xai tafi part din Inna hannunsa rike da leda, Mujaheed ya ja baya da sauri, ita ma hakan tayi, tunda Abba ya kallesu sau daya ya dauke kai, sai da ya isa daidai su.. Mujaheed ya sunkuyar da kai cike da karfin hali yace "Sannu da dawowa Abba" Abba yace "Yauwa Muhammad ya family" Imaan ta sunkuyar da kai ita ma tace "Ina yini Abba" Abba ya amsa sannan ya wuce xuwa part din Inna. Imaan ta kalli Mujaheed tace "Yaya mu je plss ka gaya min" Bata jira cewarsa ba ta kama hannunsa ta xaga baya da shi, ta xauna kan wani dakali tana nuna masa gefenta tace "Oya xauna" murmushin karfin hali yyi ya xauna, ya jinginar da kansa da nata yana kallonta ta gefen ido, tace "Toh ina ji, tell me what's it kuma ka gaya ma su Abba kuwa??" Mujaheed ya jawota jikinsa murya can kasa yace "No I didn't, and it's too late" kallonsa kawai Imaan take, kafin tace komai yace "Kin ga kayan ki da aka kawo?" Rufe fuskarta tayi da sauri a shoulder dinsa tace "Ni baxan iya ba" ya lumshe ido ya bude, a hankali yace "Yanxu dai aure kike son yi ki tafi ki bar ni koh?" Ta xaro ido tace "Toh ae kai ma kayi auren ka tafi ka bar ni" yace "Ance maki ina son auren nawa ne?" Yar dariya Imaan tayi tace "Ehh baka sonta but you are enjoying ur marriage, kuma tana haifa maka beautiful baby like her xaka fara sonta sosai" kallonta yake ko kiftawa babu, cikin sanyin murya yace "Why did u say I am enjoying my marriage imaan, how did you know??" Tana murmushi tace "Ae na gani..." da sauri yace "Kika ga me??" Taki yarda ta kallesa tace "Abinda na gani" Bai san lkcn da ya rungume ta ba yace "Noo imaan, I can neva enjoy my marriage with Safeenah, am only trying my best in fita hakkinta, ni kadai nasan abinda nake ciki imaan, bana son Safeenah, warce nake so na kokarin kubuce min which I won't allow in sha Allah" Imaan tace "Wai Aunty Farida, she told me her wedding is next week ai, xan ma je tare da Maimoon" Ya runtse ido yace "I have never loved farida, tausayinta kawai nake, kuma burina a da in hada ta su xauna da wacce aka halitto ni domin ta, sbda lalurorinta, ita ce macen da nake ma son da ni kaina ban san irinsa ba Imaan" da surprise imaan ke kallonsa jin yace baya son Farida, a hankali tace "Who is this lady Yaya? Ni ban santa ba, you've never tell me anything about her, ita ma a kd take?" lkci daya idanuwansa suka kada sosai, cikin sanyin murya yace "Na fara mata so na yan uwantaka, sannan na kasance mai tausayinta matuka, ni kaina ban ta6a tunanin soyayyar da nake mata xai rikide ya koma so na aure ba, tun bata san kanta ba nake sonta nake mata hidima, na kuma koya mata sa6o da ni...." Imaan dake ta kallonsa ta xaro ido kamar xa su fito tace "Kamar dai yanda muka sa6a ko, To wacece kuma a Ina take yaya?" Mujaheed ya dinga kallonta, Ta turo baki tace "Ni dai ka gaya min, kuma tasan kana sonta kuwa?" Ya girgixa kai a hankali yace "Taki ganewa har yanxu" Imaan tayi murmushi hade da tagumi tace "Toh nawa xaka biya ni sai ka hada ni da ita in fallasa mata sirrin dake xuciyarka, Yayana kasan fa you are very handsome..." Sai kuma ta fashe da dariya ta boye fuskarta a jikinsa tace "Wllh kana da kyau, and you are a gentle man, tall, huge, your beards are cute, so babu macen da xata iya resisting love din ka stop being afraid xaka rasa ta, kila da gudu ma xata amince maka idan ka sanar mata, wa ya sani ma ko ita ma tana sonka, it's bcos of ur handsomeness and ur personality wannan rubabbiyar matar taka ke rawan kai a kanka, take ma mutane walakanci, wllh sonka take kamar ta mutu, bata san you are only managing and just enjoying...." Sai kuma ta yi shiru da sauri, Bai san lkcn da yyi wani murmushi ba har sannan yana kallonta ya dago kanta taki yarda su hada ido yace "Enjoying what?" A rikice tace "A'a ba haka xance ba fa...." Ya lumshe ido yana shakan kamshin gashinta daga cikin hijab din jikinta murya can kasa yace "I will enjoy soon with my lil sis, amma ba da Safeenah ba...." imaan ta bude ido da sauri ta kallesa tace "Wacece?" Ya bude ido shi ma yace "Ita warce nake so mana" imaan tace "Toh are you paying me to help you out?" Yace "Ko nawa kike so kuwa, amma before then sai kinyi kokarin sa su Abba a dakatar da maganar kawo sadakin ki next week" da mamaki tace "Why? My being betrothed won't stop me from helping u out yayana" Ya girgixa kai cikin sanyin murya yace "Shine babban abinda xai sa ki kasa taimakona Imaan" Ta xaro ido tace "Yaya kai fa ka riga kayi auren ka, to ni baka son nayi auren?" Ya kalleta yace "Auren dai kike son kiyi ki bar ni" dariya tayi sosai tace "Kai ma ai ka yi" yace "Amma ai ina xuwa ganin ki kullum" tace "A'a ni dai ba wajena kake xuwa ba, wajen Inna kake xuwa" yana kallon kwayar idonta a hankali yace "Wllh duk ranan da na xo gida ban ganki ba bana iya bacci da daddare" Da mamaki Imaan ke kallonsa tace "Saboda me?" Ya sauke idonsa bai ce komai ba, tayi murmushi tace "Kaga da matarka na sona sai in koma gidan ka in yi waec a can" ya kalleta da sauri yace "A'a ba ruwanki da ita ki dawo kiyi waec din ki kawai" ta make kafada tace "Bana so, Ni fa da gaske Yaya bana son matar nan taka, I so dislike her" Yyi shiru bai ce komai ba, can tace "Yaya na fara jin yunwa fa, xaka bani lambar yarinyar ne yanxu in kirata mu yi magana?" Ya girgixa kai yace "A'a sai dai in kai ki wajenta" tace "When?" Yace "Ko xuwa gobe" tace "Toh Allah ya kai mu" da sauri ta daga kafarta tana kakkabe hijab dinta tace "Wllh Yaya sauro a nan" Mujaheed ya kunna fitilar wayarsa yana haska kafar yace "Sorry dear" yayi stretching legs dinsa ya daura nata a kai bayan ya daga hijab din yana duba inda sauron ya cije ta, shafa smooth leg din nata ya shiga yi yana kallonta, ta xaro ido ta buge hannunsa tace "Aa ni bana so Yaya" a hankali yace "Why?" Ta turo baki tace "Uhn ni bana so" tana fadin haka ta sauke kafarta kasa ta mike tace "Toh sai goben Yaya" ya mike yana kallonta yace "Mu tafi eatry tunda kina jin yunwa?" Ta juyo da sauri tace "Da gaske Yaya" yana murmushi yace "Sure, tafi ki jira ni gun mota a waje" tana murmushi tace "Toh" daga haka ta wuce ya bi ta da kallo har tayi nisa, ya lumshe ido ya bude, kamar mai tausayin kasa ya dinga tafiya har ya fita compound din ya sameta kusa da motarsa tana jiransa, yana bude motar ta shiga front seat, shi ma ya shiga maxaunin driver tana kallonsa tace "Yaya ni kaza nake son ci da drink kawai" yace "Ba sai mun je eatry ba knn" tace "A'a can xa mu je" suna isa wani eatry babba yayi ordering abinda tace, suna xaune wayarta a hannunsa tana kallon hotuna shi kuma sai kallonta yake, hotunan da suka yi tare ne kadai a camera dinsa, sauran duk WhatsApp images ne, hoton Safeenah ko kwaya daya babu a wayar tasa, Imaan ta daga kai suka hada ido, ta xaro ido tace "Why are u staring at me that way?" Bai ce mata komai ba yana kallon waitress dake ajiye masu gasasshen kaza daya da aka yayyanka sae kamshi yake, Mikewa Mujaheed yyi ya tafi ya wanke hannu ya dawo, imaan har ta bude drink din ta fara sha, ya xauna ya dau tsoka daya yana kallonta yace "Bude bakin" dariya tayi tace "Cikin mutane??" Yayi shiru yana kallonta, a hankali ta bude bakin ya kai mata naman dai dai lkcn da suka hada ido da Sadeeq dake xaune eatry din da wani frnd dinsa. *Imaan isn't for free* it's 300 via Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah Then u show ur evidence of payment via my WhatsApp number 07087865788Imaan ta sauke idonta kasa a hankali ta cire naman daga bakinta ta mayar ta ajiye, kallonta kawai Mujaheed yake ganin abinda tayi yace "What happened?" Ta turo baki taki cewa komai, Ido hudu suka yi da Sadeeq dake kallonsu har sannan shi ma, Sadeeq na ganin haka ya mike ya iso inda suke yana murmushi ya dafa table din a hankali yace "Good evening" sai a sannan Mujaheed ya sake kallonsa for d second time yace "Same to you" Imaan dai ta kasa kallonsa sai bugawa xuciyarta yake, Ya ja third chair dake wajen ya xauna yana kallonta da murmushi yace "How are you doing" Bata iya ta kallesa ba cikin sanyin murya tace "Ina yini?" Yace "Lafiya lau, kina ta enjoying da yayan ki" Mujaheed dai sai cin namansa yake ba tare da ya kallesa ba, imaan ta ki cewa komai sai wasa da ring din finger dinta take, Sadeeq na murmushi ya kalli Mujaheed yace "Ya family?" Mujaheed yace "Alhmdllh, do you care joining us..." Sadeeq na kallon naman yace "Ohh Alhmdllh, I just finished eating now" daga haka ya mike yace "Alright, xan wuce, i was about leaving na gan ku" Yana magana yana ma abokinsa sign ya taso su wuce, Mujaheed yace "Ohk then" Daga haka Sadeeq ya kalli Imaan yace "Toh malama, sai anjiman ku" ta kallesa suka hada ido, da sauri ta sunkuyar da kanta a sanyaye tace "Toh sai anjima" juyawa yyi ya bi bayan frnd dinsa da har ya nufi door din fita, Mujaheed ya kalli Imaan da ta wani hade rai ya dai ci gaba da cin namansa bai ce mata komai ba, bayan few minutes a hankali tace "Ammi xata fara nemana yanxu" ya kalleta yace "Toh wa xai ci maki naman da kika sa na siya?" Ta turo baki tace "Ni bana ci kuma" Bai tanka ta ba ya kira waitress ya sa tayi masa take away din kazar, ya tafi ya biya bill din ya dawo rike da ledan naman ya dau drink dinsa ba tare da ya kalleta ba yace "Tashi in maida ki gida" Mikewa tayi fuska daure ta bi bayansa don har ya nufi hanyar fita, bude front seat tayi xata shiga suka yi ido hudu da Sadeeq dake tsaye gun masu suya dake wajen, dauke kansa yyi ya ci gaba da yi ma mai suyan magana, A hankali Imaan ta shiga front seat din, Mujaheed ya shiga maxaunin Driver ya tada motar suka bar haraban eatry din, Har suka isa gida bai ce mata ba ita ma bata ce masa ba, Yana parking a waje ta bude motar xata fita ya riko hannunta a hankali, kamar jira take ta fara shesshekan kuka tana kallonsa, lkci daya ya rikice mata yace "Kuka kuma Imaan, what's wrong, me ya faru..." Cikin rawar murya tace "Toh ba Sadeeq ya ganmu ba yanxu, Kuma...." Sai kawai ta fashe da kuka sosai tana kallonsa, ya lumshe ido ya matso da ita kusa da shi a hankali yace "Kuma me?" Tana shessheka tace "Let him not think something different alhalin kai yayana ne kowa ma ya sani" shiru yyi yana sauraranta, jin shirun yyi yawa ta daga kai a hankali tana kallonsa, yyi murmushin karfin hali yace "Toh ba gashi kin fadi abinda ke kike tunani ba da sauran mutane, wato ni yayanki ne, to shi ma you just assume hakan xai yi tunani ni yayanki ne, tunda Ammi da Daddy ne suka haifeni sannan suka haife ki" ta turo baki tana kallonsa tace "Toh kai ba yayana bane?" Yace "Ehh in dai Ammi ce ta haifeni" ta wani hade rai tana kallonsa tace "Kamar ya?" Yace "Kamar yanda na fada" tace "To waye dama bai san kai yayana bane" Yana shafa kansa yace "Waye dai bai san ni cousin din ki bane" ta xaro ido tace "What did you mean??" Yace "I mean ki daina cewa ni yayanki ne so as people will stop thinking we are from the same parent, we are only cousins imaan, anything can happen" tabe baki tayi ta bude motar xata fita ya kamota yana kallonta yace "Wait" tsayawa tayi har sannan bata daina kallonsa ba, ya bude ledan naman ya dau daya ya kai bakinta, turo bakin tayi ta dauke kai cikin sanyin murya yace "Plss..." Tace "Toh ba kace kai ba yayana bane" yayi murmushi yace "Ehh ni yayanki ne, amma hakan ba yana nufin iyayen mu daya ba, yau idan aka ce in aure ki, baxan ce A'a ai kanwata ce ita ba, kowa yasan there is marriage between us, so stop confusing people" kallonsa Imaan take ko kiftawa babu, a hankali yace "Oya bude bakin" ta sauke idonta kasa ta ki bude bakin kuma, ya kamo hannunta yace "Imaan" kallonsa ta kara yi, ya jawota kusa da shi idonsa cikin nasa yace "Open ur mouth" a hankali ta bude bakin tana kallonsa ya kai mata naman ciki, ta gutsura kadan ta dauke kai, yana murmushi ya kai sauran baki yace "Toh shkkn kanwata" Bude motar tayi tana son fita yayi saurin riketa yace "Since I got married nake missing din ki sosai unlike before da nake gida that we are always fighting, from now on every magrib idan kin je kai ma Inna abincin ki jira har sai na xo mun yi hira kadan kafin na wuce kin ji" tayi murmushi tace "Toh ai da haka muke yi kafin ka canxa ka fara ma mutane fada da ihu" ya kai tip din finger dinsa kan lip dinta murya can kasa yace "Na daina yanxu dear, hira kawai xan dinga xuwa muna yi, sai in taho maki da abun dadi" ta wara ido tace "To Yaya, xan dinga jiran ka" ya daure ledan naman da drink ya mika mata yace "Good girl" ta amsa tace "Toh nagode, sai da safe" yace "Sleep tight" ta fita motar tana murmushi ta wuce ciki ya bi ta da kallo. Parlor ta tadda Ammi tana cin abinci, Ammi na kallonta tace "Me yasa kika dade, kuma ledan meye hannun ki?" Imaan ta xauna tace "Yaya ne ya siya min" Ammi tace "Yaya kuma, a kan me ya siya maki?" Tace "Ba komai, kawai dai ya siya min ne ya bani ai yasan ina so" Ammi ta tabe baki ta ci gaba da cin abincin ta, Imaan ta bude ledan tace "In debar maki Ammi?" Kamar jira Ammi take tace "A'a ki je kiyi ta fama" Imaan tayi dariya ta mike ta wuce kitchen ta dauko plate ta juye naman taci taci ta sha drink tayi nakk, sauran ta kai fridge tana kallon Ammi tace "Ammi sai da safe" Ammi tace "Allah ya tashe mu lafiya, don't forget perform ablution before going to bed, kuma kar ki manta kiyi addu'a, kin ma yi isha kuwa??" imaan tace "xan yi yanxu Ammi" daga haka ta wuce dakinta, wanka tayi ta dauro alwala ta fito ta shirya cikin kayan bacci ta sa hijab har kasa tayi isha da shafa'i, tana idarwa ta dau wayarta dake gaban mirror tana dubawa, xaunawa gefen gado tayi ta shiga kiran Sadeeq don duk dare sai ya kirata yau kuma bata ga call dinsa ba, har ya gama ringing bai dauka ba, Ajiye wayar tayi a hankali ta hau saman gado ta kwanta ta rufe ido. Karfe biyar saura na yammacin washegari Ammi na xaune parlor tana yankan pumpkin leaf aka bude kofar parlon Mujaheed ya shigo da sallama, ya ajiye ledojin hannunsa na kayan shayi ya gaida Ammi ta amsa tana masa sannu da xuwa yace "Daddy yace a kawo sakon" Ammi tace "Ohk Yusuf baya nan kenan" Mujaheed yace "Ehh Ina ji" tace "Toh Allah yyi albarka" yace "Ameen" har ya nufi kofa ya tsaya ba tare da ya juyo ba yace "Imaan bata dawo schl ba?" Tace "Bata je yau ba" ya juya da sauri yace "Me yasa?" Ammi na ci gaba da yanka leaf din tace "Yau ta tashi ba lafiya" Yace "Subhanallah, likita ya xo dubata amma?" Ammi ta girgixa kai yace "Ynxu likitan ba wai yana xama bane, yana Sokoto yau, amma gobe xai dawo, mun dai je asibiti" yace "Bacci take?" Ammi tace "Ina ji" shiru yyi bai ce komai ba, Ammi ta kallesa hakan yasa ya nufi kofar fita kamar mai counting steps dinsa yace "Toh Allah ya bata lfya" Ammi tace "Shiga ka duba ko idonta biyu" Kamar abinda yake jiran ji kenan ya juya ya nufi dakin Ammi ta bi sa da kallon gefen ido har ya shiga sai dai bai rufe kofar ba. Kwance ya sameta ta rufa har kanta da duvet, ya xauna gefen gadon ya cire duvet din yana kallonta, tun bai kai hannunsa jikinta ba ya ji temperature dinta is so high, ta bude idonta da yyi ja tana kallonsa, kamar xata yi kuka ta fara kokarin mikewa xaune tace "Yaya jikina xafi yake min sosai kuma Ammi ta ki bari in kunna fan ko Ac" sai kuma ta fara kuka, ya jawota kusa da shi murya can kasa yace "Why did u cover ur self?" Cikin rawar murya tace "Am feeling cold" yace "Kuma shine kike son kunna fan" Bata ce komai ba sai kuka take a hankali, ya daga kanta yace "An maki allura da ku ka je asibitin?" Kai ta gyada masa tace "My legs are still aching har yanxu da bayana" yace "An shafa maki magani kuma?" Ta gyada masa kai tana goge hawayen idonta, janyeta yyi jikinsa ya dau Magungunan dake ajiye side drawer har da na shafawa, ya mayar da saura ya bude na tube din ya cire gaba daya duvet din, daga kneel dinta ya fara shafa mata xuwa toes dinta, ta dinga kallonsa kamar xata yi kuka tana rike hannunsa tace "Yaya xafi" daga kai tayi taga Ammi tsaye bakin kofar dakin, Mujaheed ya juya ya kalli kofar, juyawa Ammi tayi ta bar bakin kofar, Imaan tace "Ka bar shi haka kawai ya fara min sauki" Ya rufe tube din yana kallonta, jin wayarta na vibrate ta juya da sauri ta dau wayar, Sadeeq ne ke kiranta, dagawa tayi ta kai kunne tayi sallama a hankali, Daga daya bangaren ya amsa, ta gaishesa, yace "How are you doing" cikin sanyin murya tace "Lafiya lau, why ain't you picking ur calls" yace "Ba gashi Ina following calls that I have missed ba ynxu" shiru tayi, shi dai Mujaheed kallonta kawai yake, Sadeeq yace "Ya Ammi?" A hankali tace "Lafiya lau" yace "Maa sha Allah, we will talk later sai anjima" daga haka ya katse wayarsa, ajiye wayar Imaan tayi Mujaheed na kallonta yace "Kiransa kika dinga yi knn?" Bata san lkcn da ta fashe da kuka ba ta kife kanta da pillow tace "Kila fa fushi yake da ni Yaya, it's very unusual bai kirani ba tun jiya" Kasa daina kallonta Mujaheed yyi, tana shessheka tace "I called him sau biyu bai dauka ba, tun ba yau ba nake ce masa kai yayana ne ko ya xatan karya nake masa, Yaya plss kai ka gaya masa da kanka kila xae yarda, we are just close with you and nothing more, kai yayana ne" Mujaheed na kallonta a hankali yace "We are just close and nothing more, what if it's totally not so imaan kamar yanda shi yake tunani?" Ta daga kai da sauri tana kallonsa tace "Toh ai ni da kai mun san ba haka bane Yaya, an taba ganin inda Yaya ya auri Kanwarsa??? Hakan bai ta6a faruwa ba, don Allah Yaya make him understand this, I am just sick of this, ni bai taba min haka ba" Mujaheed yyi wani murmushi yana shafa kansa yace.... Sorry for the short chapter... don't forget i am still not home but I am managing to type, in sha Allah xuwa karfe tara da wani abu ltr xa ku ji ni. Thank you. *Imaan isn't for free* it's 300 via Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah Then u show ur evidence of payment via my WhatsApp number 07087865788Mujaheed yyi wani murmushi yana shafa kansa a hankali yace "Saboda bai dau wayarki ba shine kika fara leg and backache kenan??" Banxa tayi masa ta koma ta kwanta ta juya masa baya, ya dinga kallonta ko kiftawa babu kafin ya mike ya nufi kofa yana murmushi ta bi sa da harara har ya fita ya rufe mata kofa. Tun daga wannan rana Sadeeq ya daina kiran Imaan gaba daya sai dai in ita ta kirasa, sosai ta shiga damuwa ta rasa me ke mata dadi, ko abincin kirki bata iya ci, bata taba tunanin akwai abinda xai daga mata hankali haka ba, ko da yaushe a sanyaye xaka ganta, tana wanke wanke a kitchen ranan Thursday da yamma Ammi ma na kitchen din tana kwashe shinkafar da ta dafa a warmer, tarwatsewan glass cup da ta ji yasa ta juya da sauri tana kallon Imaan da ta koma baya tana xaro ido, don na biyu kenan ta fasa tsayuwarta a sink din, Ammi ta daure fuska cikin tsawa tace "Are you stupid imaan, tunanin uban me kike kika sake fasa min wani cup din?" Hawaye imaan ta fara yi tana kallonta, Cikin tsawa Ammi tace "Get out kar in gaura maki mari my friend" juyawa Imaan tayi da sauri ta fita, Ammi ta gama kwashe abincin ta tafi ta ci gaba da wanke wanken, tana gamawa ta fita xuwa dakin Imaan, Kwance ta ganta ta rufe fuskarta da pillow, har ta karasa kusa da ita ta xauna gefen gado bata sani ba, Ammi tace "Imaan..." Da sauri ta dago a tsorace don bata ji shigowar ta ba, sai kuma ta fara goge idonta tana sunkuyar da kanta, Ammi ta kamo hannunta cikin sanyin murya tace "Tell me what's wrong with you plss Imaan, kina da wata da xaki fada ma damuwarki ban da ni, am asking you this for the third time, kar ki yarda in kira daddy yanxu kin san dawowa xai yi" Imaan ta fashe da kuka sosai ta rungume ta, lkci daya jikin Ammi yyi sanyi, ta dago kanta cike da damuwa tace "Ki gaya min damuwarki daughter" cikin rawar murya tace "Ammi mai sunan Daddy ne...." Da mamaki Ammi ke kallonta lkci daya kuma gabanta ya fadi don right from time ta gudar ma only child din tata heartbreak, cike da karfin hali tace "What about him???" Cikin kuka Imaan tace "He is calling me no more, ko na kirasa baxai dauka ba sai washegari" Ammi dake kallonta duk da tashi da hankalinta yyi ta dake tace "Me ya hada ku?" Shiru Imaan tayi hawaye na sakko mata, bata ma san me xata ce ma Ammi ba, tasan ko hauka take baxata ce don ya ganta da Mujaheed a eatry bane Mujaheed na bata nama a baki, ta hadiye abu da kyar tace "Kila saboda yana ganina tare da Yaya ne always" Ammi tace "Toh dole sai kin tsaya tare da Yaya, Ina ruwanki da shi da yyi aurensa, wato yana ganinku kuna shashancin da ku ka saba kina xaunawa kusa da shi ko???" Imaan ta fashe da kuka a hankali tace "Wllh Ammi na daina haka ai" Ammi bata iya tace komai ba, imaan ta kamo hannunta cikin rawar murya tace "Ammi ko xa ki kirasa ki masa magana don Allah" wani kallo Ammi ta mata tace "Ba mu gaji haka ba ai, ni ba gantalalliya bace, kuma bari in gaya maki ba a ma namiji son hauka, kawai don bai kula ki ba ki wani damu ki daga hankalinki kisa ma kanki wani cutar ki cuce ni?" Ta rufe fuskarta a kafar Ammi tana shessheka tace "Ammi wllh da gaske Ina son sa" Ammi ta dinga kallonta, can ta dago kanta cikin sanyin murya tace "Ki kwantar da hankalin ki Imaan, amma bana son kina damuwa, kin basa hakuri kuma?" Imaan ta girgixa mata kai, Ammi tace "Toh ki kirasa ko ki masa text ki basa hakuri, sai ke kuma ki kama kanki ba ruwan ki da wani Yaya from now on kin ji abinda nace?" Imaan ta gyada mata kai a hankali, Ammi tace "Kuma ban ce ki gaya ma Inna ba" a hankali Imaan tace "Toh Ammi" Ammi tace "Ta shi mu je ki xuba abinci yanxu" ba musu Imaan ta mike ta bi bayan Ammi suka fita dakin. Karfe shidda Imaan ta tafi kai ma Inna abinci don bata ma son ta je da Magrib ta hadu da Mujaheed, turo baki tayi ganin takalma bakin kofar, ta shiga da sallama ba tare da ta yarda ta kalli wanda ke xaune a parlon ba ta ajiye abincin, Inna na washe baki tace "Toh kin kawo a dai dai kuwa, kawo plate in dibar masa nasan baxai wuce shinkafa ba dai" Imaan ta saci kallonsa lkci daya gabanta yyi mugun faduwa ganin Sadeeq xaune parlon cikin kananun kaya idanuwansa sanye da glasses, suna hada ido ya dauke nasa idon, ta kasa fita parlon, Inna tace "Baxa ki kawo kwanon bane in tashi da kai na" Yana murmushi yace "Kaka da gaske fa na koshi, yanxu muka gama cin abinci da abokaina a gidan cin abinci" Inna ta rike ha6a tace "Toh abincin gidan naku ba dadi ne Bukar har sai ka fita gidan masu abinci?" Sosai Sadeeq yyi dariya yana kallonta yace "Kaka saboda abokaina ne muka je can" Inna ta tabe baki tace "Atoh, na ji ance fa naman aladu suke siyar ma mutane, ni dai da xaka yi hakuri ka daina xuwa idan ma girkin gidan naku ne baka so sai ka dinga xuwa nan xan saka maka a kwano in ajiye, kazamai da masu wari sun yi yawa a duniya yanxu kaje ka ci abinda xai hallaka ka wataran mu shiga uku gaba daya" Shi dai dariya kawai yake Imaan ta juya ta fita parlon.... Dai dai inda suke yawan tsayuwa da Mujaheed ta tsaya, ba a wani dau lkci ba taji foot steps dinsa yana tahowa, yana kusa isowa wajen suka yi ido hudu, yyi slowing pace dinsa amma kuma ba shi da alamar tsayawa, cikin sanyin murya tace "Plss ka tsaya Abbana" Tsayawa yyi ya dawo gefenta ya rungume hannunsa a hankali yace "Toh na tsaya daughter" Lkci daya hawaye ya kawo idonta ta sunkuyar da kai cikin rawar murya tace "Don Allah kayi hakuri ka yafe min" Yace "Inyi hakuri a kan me" da kyar tace "Abinda yasa kake fushi da ni" yayi murmushin karfin hali yace "Aa ban yi fushi ba Imaan" tace "Wlh ka yi, don Allah kayi hakuri wllh hakan baxai kara faruwa ba" Yace "Imaan don Mujaheed yayan ki ne kamar yanda kike yawan fadi ba yana nufin same parent suka haife ku ba so I have all right to get angry, Shi din ba Muharramin ki bane, da nine nace mu fita eatry ni da kudin gaisuwana ke kanki ba yarda xa ki yi ba, not to talk of giving ur meat..." ta dinga goge hawayen da ya ki tsaya mata tace "Plss kayi hakuri, baxan sake ba, abinda ma yasa ya kai ni wajen ranan ya siya min kaza shine saboda I promise xan taya sa fada ma wata yarinya da yake so cewar yana sonta wai ya kasa fada mata.... Wllh saboda nace ni xan yi ma yarinyar magana ya sa ya siya min kaza don in maya" murmushi Sadeeq yyi yana shafa kansa yace "Ya wuce Imaan... Xan wuce masallaci it's almost time" a hankali tace "Ka hakura?" Yace "Tuni na hakura ai" mu je ki raka ni gate, har suka isa gate babu wanda yace komai cikinsu, yana kallonta yace "Good night" ta gyada masa kai ya wuce ta juya ta koma ciki. Tun daga sannan imaan tayi kokarin dinga avoiding Mujaheed, ko parlonsu ya shigo dama tashi take ta wuce daki ko ta wuce kitchen, part din Inna kuwa kafin yaje xata kai mata abinci ta maxa ta dawo, ana haka har ya rage two weeks su fara exams kuma hakan yyi dai dai da saura sati biyu a kawo lefenta tare da sadaki daga gidansu sadeeq, sosai ta dage da azkar kamar yanda Ammi ta ce mata saboda yawan faduwan gaba da take, Ammi ma ta bata addu'o'in da xata dinga yi tana kuma kokarin tashin ta duk dare tayi sllh. Yau Saturday Imaan ta fito parlor sanye da hijab dinta har kasa hannunta rike da karamin jaka, duk da babu komai fuskarta sai eye pencil da Chappete ba karamin kyau sanyanye tayi ba, Ammi dake xaune parlor ta bi ta da kallo har ta durkusa kusa da ita tace "Ammi xa mu wuce" Ammi ta d'an yi shiru kafin tace "Kar ki dade Imaan, ko minti goma plss kar ki yi ba mutuncin ki bane, kina yin abinda ya kai ki ki juyo" Imaan ta d'an yi murmushi tace "Toh Ammi in sha Allah" Ammi tace "Ko xa ku dawo napep xa ku hau kin ji abinda nace koh?" Imaan tace "Toh Ammi" daga haka ta fita parlon, ta nufi part din su Maimoon, a hankali ta bude kofar ta shiga da sallama murya can kasa, Umma ce xaune parlon, sai Mujaheed dake xaune shi ma ya jinginar da kansa da kujera idonsa lumshe, Safeenah ma na xaune parlon tana taunar cingam, Umma tace "Toh ni na ta6a jin rashin lafiya haka, bari Abbansa ya shigo kila idan yyi masa magana xai yarda a dubasa, su dama likitocin nan haka suke da shegen taurin kai sai dai su duba wasu ba dai a duba su ba" Safeenah ta tabe baki tace "Wllh kuwa Hajiya, har ce min yake ba ruwana in daina sa masa ido, Toh ya baxan sa ido ba mijina ba lafiya, ko abinci bai ci fa Umma sai dai coffee da tea mun fi sati a haka" Umma ta rike ha6a tace "Ba lafiya kuwa, bari Abba ya shigo wannan ai ba yi bane" Imaan da ta sunkuyar da kanta ta nufi stairs tace "Ina yinin ku" babu wanda ya tanka ta a parlon har ta wuce sama, Umma ta kalli Safeenah, Safeenah tayi wani murmushi tana kas kas da cingam, Mujaheed tunda ya ji muryarta ya bude ido, ba a dau lkci ba Imaan ta sakko tare da Maimoon dake sanye da hijab ita ma har kasa, suna shigowa parlor Umma ta bi su da kallo, Maimoon tace "Sai mun dawo Umma" Umma tace "Yauwa" Imaan dai bata juyo ba har ta fita, Maimoon ma ta fita, Mikewa Mujaheed yyi yana kallon Umma yace "Bari in je in gaida Inna in dawo yanxu" Safeenah ta mike tace "Ehh bari mu je Umma yanxu xan dawo sai mu fita kasuwan" wani kallo Mujaheed ya dinga mata fuska daure yace "Da can baki san xa ki part din Inna ba sai da nace xan je??" Safeenah ta tabe baki ta nufi kofa tana gyara mayafin jikinta ya bi ta da kallo, imaan da Maimoon na isa bakin titi suka tsayar da adaidaita, Imaan na kallon Maimoon tace "Wllh ban san me yasa gabana ke faduwa ba tun daxu Maimoon" Maimoon tace "Haba dai, to ki dinga addu'a" Imaan tace "Ehh Ina yi" daga haka ta kalli mai adaidaitan da suka tsayar.... *Imaan isn't for free* it's 300 via Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah Then u show ur evidence of payment via my WhatsApp number 07087865788A hanya imaan ta sa mai adaidaitan ya tsaya gun masu fruits ta siya fruits kusan kala hudu sannan suka koma adaidaitan, Tafiyar kusan minti ashirin suka yi suka isa wani babban hospital wanda kai kana gani kasan na masu hali ne, sauka suka yi a adaidaitan kafin Imaan ta basa kudi daga cikin jakarta Maimoon ta basa, hakan yasa Imaan ta ciro wayarta kawai ta shiga kiran layin Mariya, ba a dau lkci ba Mariya ta daga, Imaan tace "Muna waje" Mariya tace "Ohk to gani xan fito yanxu" Imaan ta mayar da wayar jakarta suka shiga haraban hospital din, ba a dau lkci ba Mariya ta fito ta nufo su tana murmushi suka gaisa da fara'a suna tambayarta me jiki, Mariya tace "Da sauki sosai, mu shiga ciki" bin bayanta suka yi har xuwa special ward din da aka kwantar da step sis din nata, da sallama suka shiga cikin babban ward din mai dauke da gado daya sai kujeru da karamin Tv na bango, ga labulaye a duk windows din, gadon ma kadai dake dakin ya isa ya bayyana cewa ward din na special people ne, Mahaifiyar Sadeeq Hajiya Khadijah ce xaune saman kujera, sai Aunty da frnd din Mum din Sadeeq da kanwarta, Aisha kanwar Sadeeq na kwance saman gadon tana bacci an sa mata drip, sai autar su Sadeeq din dake tsaye hannunta rike da incense da ashana, Imaan ta sunkuyar da kai ta karasa cikin dakin da ladabi ta gaida su, Hajiya Khadijah ta amsa tana kallonta, Aunty da sauran mutanen ward din ma duk suka amsa, Aunty na nuna masu kujera tace "Toh ku xauna" Maimoon ce ya fara xama, Imaan kuwa sai da sister din mahaifiyar sadeeq ta sake maimaita mata ta xauna sannan ta xauna har sannan kanta na kasa, Mariya na murmushi tana kallon stepmother dinta tace "Mummy ita ce budurwar ya sadeeq warce xai aura fa...." Mummy na kallon Imaan da kyau tace "Wannan ba warce ku ka yi sauka tare bane kwanaki har muka yi hotuna" Mariya tayi dariya tace "Ita ce Mummy ashe dai xa ki gane ta" Aunty dai sai murmushi take tana kallon Imaan da ta kasa dago kai gaba daya she was uncomfortable ba kadan ba, Mummy ta d'an yi murmushi tace "Toh Maa sha Allah, Allah ya sanya albarka..." Mariya tace "Ameen, amma fa tun kafin saukan suke tare Mummy" Mummy tace "Toh maa sha Allah, hakan yyi kyau" Aunty na kallon Imaan tace "Ya su mamanku" a hankali tace "Tana gaishe ku" Aunty tace "Toh mun gode Allah maku albarka" duk suka amsa da "Ameen" a hankali Imaan ta dago kai tana bin ward din da kallo jin numfashinta na d'an tsarkewa, kanwar Sadeeq ta gani xaune chair din dake kusa da wanda ta xauna hannunta rike da incense har stick biyu ta kunna, Imaan ta kauda kai, sai kuma cikin dubara ta dan rufe hancinta da hijab din jikinta, Lkci daya Maimoon ta lura da hakan, ta taba ta murya can kasa tace "kiyi masu sallama mu wuce kawai" kasa cewa komai Imaan tayi, su Aunty dai hiransu kawai suka ci gaba da yi, Maimoon ta mike tana kallonsu tace "Toh mummy xa mu koma, ga wannan a ba mara lafiya, Allah ya bata lafiya" tana magana tana ajiye ledan hannunta a table, Aunty tace "Har xa ku tafi, to mun gode Allah ya saka da alkhairi" Mummy tace "Toh mun gode, ku gaida gida da mutanen gida" tuni Maimoon ta kama hannun Imaan tana amsa masu da Ameen, Mummy na kallon Imaan da murmushi tace "Toh ya sunan naki?" Maimoon tace "Fatima Imaan" Imaan ta warce hannunta daga rikon da Maimoon ta yi mata ta nufi kofa da sauri dai dai lkcn da aka bude kofar ward din Sadeeq ya shigo, bata kai ga fita ba ta durkushe bakin kofa ta fara gasping for air tana tari, Mariya da Maimoon suka nufeta da sauri, Su Aunty da Mummy ma duk suka mike suna salati suka nufeta, Sadeeq ya xura wayarsa aljihu ya durkusa kusa da ita ya dagota yana kallonta yace "Subhanallah, Imaan are you okay..." Mariya ta kashe incense din hannun Step sis dinta, a nan kuma duk suka dago musabbabin tashin Asthma din nata, ba karamin tausayi Imaan xata baka ba ganin yanda take struggling da numfashin nata a kasa, gaba daya su Mummy da Aunty da mutanen dake ward din duk suka rikice, Maimoon ta durkusa ta cire jakarta dake rataye shoulder dinta ta bude da sauri tana bincika ciki ko akwai inhaler amma taga babu, ganin haka Sadeeq ya daga ta ya fitar da ita daga ward din, Aunty ta bi bayansa ita ma hankali tashe Maimoon da Mariya ma suka fita, cike da damuwa Mummy tace "Ai ba a san she is asthmatic ba, da Suhaila bata kunna turaren ba, kuma duk sai suka yi shiru basu ce komai ba" Kanwar Mummy tace "Wllh kuwa, irin haka ai magana xa su yi, gashi an ja mata wahala yanxu" Kawar Mummy tace "Ikon Allah shi kuma Sadeeq ana neman mai lafiya ya jajibo ma kansa ciwo Allah na tuba, dubi fa d'an hayakin da ya tada Asthma ni fatima Allah na tuba, kenan wannan dai ko shara bata yi balle aje ga soye soye a kitchen, don in dai wannan hayakin xai iya tada Asthma to fa babu abinda baxai tayar ba, Toh Allah dai ya kyauta, Allah kuma ya bata lafiya" Mummy dai bata ce komai ba haka kanwarta da ta mike ta bi bayansu Aunty. Sadeeq na xaune gefen Imaan dake kwance daya daga ward din hospital din, ban da juye juye babu abinda take yi har sannan da kyar take numfashi, Aunty sai sannu take mata tana kallonta cike da tausayinta, Mummy dai na tsaye jikin window ta rungume hannu tana kallonta ita ma, Mariya har da d'an hawayenta, Maimoon na kusa da sadeeq ta kama hannunta tana tofa mata addu'a a hankali, wani likita ne ya shigo ward din yana kallon Imaan yace "Sit upright now" Sadeeq ya mike don ta samu ta tashi xaune, da taimakon Maimoon ta xauna, likitan yace "How are you feeling now" Bata iya tace komai ba, A hankali Sadeeq yace "She said her chest..." Murmushi likitan yyi ya dafa Sadeeq yace "Anya kuwa Dr idan emergency ya tashi gidan ku cikin dare xaka iya ta6uka abun kirki?" Aunty ta ta6e baki tace "Haka nan yake wllh Dr, ni ban ta6a ganin likita haka ba, gaba daya mance cewa shi likita ne yake in a situation like this" Dr din ya d'an yi dariya yace "Gaskiya ne..." Ya maida dubansa gun Imaan da ta hade kanta da pillow yace "Amma an ta6a maki allura idan Asthma din ki ya tashi ba inhaler a kusa?" Bata tare da ta dago ba ta gyada masa kai da kyar, Yace "Toh Allah ya sauke, xai daina in sha Allah mun baki magani ai... Allah ya baki lafiya" Ita dai bata ce komai ba, likitan na kallon Sadeeq yace "Nan da few hours xa a sake shigowa duba ta Dr... Allah ya tsare, sai a dinga kiyayewa" Sadeeq ya d'an yi murmushi yace "In sha Allah" daga haka likitan ya fita yana kara gaida su Mummy, Sadeeq ya duka yana kallon Imaan, murya can kasa yace "Sorry dear" ita dai bata ce komai ba, yace "Toh kwanta da kyau" sai a sannan ta dago kanta a hankali ta kwanta tana sauke numfashi a hankali, Mummy dai sai kallonta take haka ma Aunty, can Mummy tace "Toh Allah ya sauke, bari in koma daya ward din" daga haka ta fita, Aunty ta ja kujera ta xauna, nan da nan bacci ya dauke Imaan. Maimoon dake xaune kan kujera tare da Mariya suna kallon Imaan ta fiddo wayar Imaan dake ring a jaka, number Ammi ta gani a screen, ta daga ta kai kunne tayi sallama murya can kasa, a hankali Ammi tace "Imaan din fa Maimoon?" Maimoon tace "Wlh Ammi ta sami attack ne a hospital din, amma da sauki yanxu tana bacci ma" Mahaifiyar Mariya dake ward din har sannan tana duban Maimoon tace "Kawo wayar" Mikewa Maimoon tayi ta tafi ta kai mata wayar, bayan sun gaisa Aunty tayi mata bayanin abinda ake ciki tace "Amma da sauki Alhmdllh don har tayi bacci, xuwa anjima in sha Allah xa a taho da su gida" Ammi tace "Toh maa sha Allah, an gode sosai, Allah ya saka da alkhairi" Aunty tace "A'a ba godiya Hajiya, mu ma mun gode" daga haka suka yi sallama Aunty ta mika ma Maimoon wayar, kusan la'asar Sadeeq ya shigo ward din rike da ledan drugs, Maimoon da Mariya ne kadai dakin Aunty ta tafi gun su Mummy, Har ya karasa gun Imaan kallonta yake ganin yanda ta takure waje daya, ya kai hannunsa forehead dinta, sosai ya ji jikinta da xafi, ta bude idonta da suka kada tana kallonsa, lips dinta ma yyi ja sosai, dukawa yyi da damuwa yace "Are you okay imaan, har yanxu kirjin na maki ciwo ne" kokarin tashi xaune ta shiga yi da kyar tana dafa bayanta, ya kama hannunta ya taimaka mata ta tashi, ganin yanda ta rufe ido yace "Ina ke maki ciwo??" Murya can kasa tace "I am feeling internal heat, kuma Ina jin sanyi, my back is aching" Shiru yyi yana kallonta cike da tausayi, can ya juya ya fita suka dawo tare da likita, a dakin ya tadda Mummy xata wuce gida ta dawo anjima shine ta shigo yi masu sallama, tana tsaye kan Imaan ganin yanayinta tana kallonta tace "Wani abun na damun ki ne kuma? Ko kina jin ciwo a wani waje ne?" Imaan ta girgixa mata kai da kyar bata ce komai ba, likitan ya karasa ya kai hannu jikinta yana kallonta yace "Me kike ji a jikin ki?" Imaan ta girgixa masa kai a hankali hawaye cike idonta tace "Kawai ina son xan wuce gida" Sadeeq yace "Noo ki fada masa inda ke maki ciwo" da kyar tace "Joint pain, kuma Ina jin xafi a jikina...." Likitan ya kai hannu forehead dinta yana kallonta, yace "Yana maki haka ne?" Kai ta gyada masa, yana kallon kwayar idonta ya d'an yi shiru sai kuma ya kalli Sadeeq yace "Is she a sickled cell patient?" A hankali Sadeeq ya girgixa masa kai yace "She is only carrying the trait" Likitan yace "Wani drugs kike sha a gida?" Cike da karfin hali tace "Suna da yawa" likitan yace "Did you know their names?" Sadeeq yace "I will get drugs for her now, amma ayi mata allura" daga haka ya juya ya fita ward din. Aunty ce ta sakko parlor sanye da hijab hannunta rike da purse, ta kalli Mujaheed tana amsa gaisuwar da yake mata a parlorn sannan ta kalli Umma tace "Xan fita sai na dawo Hajiya" Umma tace "Ina kuma xa ki da magariba" Aunty tace "Xan je dubiya asibiti ne" da mamaki Umma tace "Waye ba lafiya?" Aunty tace "Baki san su ba" Dai dai nan Abba ya shigo parlon yana kallon Aunty yace "Ba ku tafi ba kenan" Aunty tace "Ehh yanxu xa mu fita" Abba yace "Xuwa anjima idan anyi isha xan leka asibitin" Umma na kallon Abba tace "Wai waye ba lafiya" Abba ya kalli Aunty yace "Bata sani ba ne dama?" Aunty bata tanka sa ba ta nufi kofa, Abba ya girgixa kai yace "Imaan ce suka je duba kanwar yaron nan dake nemanta a asibiti shine Asthma dinta ya tashi, ita ma dai tana asibitin yanxu" Kallonsa kawai Mujaheed yake ko kiftawa babu, Umma ta saki salati tana tafe hannu tace "Shine ake boye min, shi ciwon Amina ke boye min fisabilillahi? Meye amfanin xaman munafurci Alhaji, wato ita ta ji xata tafi dubata a asibitin ni kuma sai uwar yarinyar da Inna su kullace ni su xata naji xuwa ne bana son yi, toh xuciyata bai kai haka lalacewa ba, kuma nima yanxu xan shirya mu tafi, sai dai ita ta ji kunya, ban taba ganin munafuka irin Amina ba wllh, duk ita ke hada ni da Aisha na lura" Shi dai Abba ko tanka ta bai yi ba ya wuce parlon sa, Umma ta wuce sama da sauri don dauko hijab, Mikewa Mujaheed yyi ya fita parlon ya bi bayan Aunty, tare ya gansu suna tahowa da Ammi dake sanye da hijab ita ma, yana tsaye har suka iso, ya gaida Ammi ta amsa tana tambayarsa ya aiki, yace "Alhmdllh, ya mai jiki" Ammi tace "Toh da sauki" a hankali yace "Toh mu je in ajiye ku" Aunty tace "Toh ka kyauta" dai dai nan Umma ya fito parlon sanye da hijab ita ma, tana kallon Aunty tace "Toh Amina xuciyata bata kai inda kike tunani ba lalacewa, rashin lafiya Kuma da ke kan kowa kike boye min fisabilillahi??" Aunty ko kallonta bata yi ba ta nufi gate, Ammi dai bata ce komai ba ita ma tafiyar take, Umma tace "Munafurci dai bashi da amfani a rayuwa, kuma tare kika shigo gidan nan kika ganmu da Aisha" daga haka ta kalli Mujaheed tace "Kai xaka kai mu ne" ba tare da ya kalleta ba yace "Ehh" har suka shiga motar tasa babu wanda yace komai, Aunty ta gaya masa asibitin bayan sun hau saman titi. Maimoon ce ta fito ta kai su har ward din da imaan take, Mummy na xaune saman kujera kusa da gadon da imaan take kwance tana bacci, sai kannin Sadeeq biyu da kanwarta da Mariya, Su Aunty na shiga ward din Mummy ta fara welcoming din su, a ka shiga gaisawa fara'a, Umma dai sai kallon Mummy take, Mummy tace "Jikin ma da sauki sosai, kawai drip din ne da bai kare ba, don sunce biyu ne" Aunty tace "Toh Alhmdllh, Allah ya sauwake, ku kuma Allah ya bada lada" Mummy tayi murmushi tace "Toh Ameen, Allah ya bata lafiya" Mujaheed dai na tsaye daga bakin kofa yana kallon Imaan dake bacci tana sauke numfashi a hankali, da sallama Sadeeq ya shigo ward din.... *Imaan isn't for free* it's 300 via Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah Then u show ur evidence of payment via my WhatsApp number 07087865788Sadeeq ya gaida su Aunty da ladabi, sannan ya gaida Umma ma dake ta kallonsa, Umma tace "Lafiya lau, ya hidima?" Yace "Alhmdllh" Umma tace "Toh Allah ya bata lafiya, ku kuma Allah ya sassaka da dawainiya, a haka nan dai ake kullum yau ciwo gobe lafiya, an rasa gane kan abun dai, Allah dai ya rabata da wannan cuta da ya ki ci ya ki cinyewa ni Rukayya" Mujaheed dake ta kallon mahaifiyar tasa ya karasa cikin ward din xuwa gadon da imaan take tana bacci ya tsaya yana kallonta, ya kai hannu goshinta ya ji babu xafi bacci dai take mai nauyi, Umma dai sai wani kallo take masa ta gefen ido, Aunty na kallon Mummy tace "Toh Hajiya tunda kuna nan mu xa mu koma, Allah ya saka da alkhairi, mun gode kwarai" Mummy na murmushi tace "Ah haba dai ba komai ai yi ma kai ne, Allah dai ya bata lafiya, ya ba mu alkhairi" Ammi ma tayi mata godiya hade da sallama, Umma da ke xaune ta ki tashi ta bi su da kallo baki sake tace "Sai kace ana koranmu ko tashi yarinya bata yi ba balle mu ga lafiyarta ku ce xa mu wuce?" Can ta tabe baki tana gyara xama tace "Atoh ku je ni sai na xo" Ita dai Ammi bata ce komai ba har ta fita Maimoon ma ta fita, Mujaheed dai sai kallon uwar tasa yake daga inda yake tsaye, Aunty dake ta kallonta ta dai nufi kofa tana danna wayarta, suna fita ward din ta kai waya kunne bayan wani lkci tace "Toh ga Matar ka can gaban surukai tana maganganu da bai dace ba a kan ciwon 'yar ka, mun fito yanxu xa mu tafi tace babu inda xata kawai dai don ta samu sararin ci gaba da rashin kirkinta a wajen, idan ma xaka kirata to ka kirata ta fito ward din nan, Banda ma kinibibi da can duk ciwon da Imaan take ta ta6a bin mu asibiti...." Bata jira cewarsa ba ta kashe wayarta fuska daure, Ammi dai sai murmushi take suna tafiya, ko minti daya ba ayi ba Abba ya kira Umma dake kallon Mummy tana cewa "Mun gode fa, Allah ya saka da alkhairi ya bada lada, abun kam sai addu'a yau ciwo gobe lafiya ana dai ta tafiya a haka..." Ring din wayarta yasa tayi shiru tana kallon screen din, can ta daga ta kai kunne kafin tace komai Abba yace "Rukayya ku dawo gida yanxun nan gaba daya" a hankali tace "Ko saboda me?" Strictly yace "Nace ki dawo yanxu Madam" tace "Toh" daga haka ta katse wayar tayi tagumi tana kallon Imaan bayan kusan minti uku ta mike tana murmushi tace "Toh, Hajiya tunda sun ce mu tafi bari mu wuce don a mota daya muke, ma dawo da safe, Allah ya saka da alkhairi" Mummy tace "Toh Ameen, Allah ya tashe mu lafiya, sai da safen" Da ido Mummy ta bi ta har ta fita kafin ta dauke kai, Mujaheed dai na tsaye kusa da gadon har sannan idonsa na kan imaan, Sadeeq dake tsaye ya ja kujera ya xauna, Mummy na kallon Mujaheed da murmushi tace "Kanwarka ce koh?" Murmushin yyi shi ma yace "Ehh kanwata ce" Mummy tace "To madallah, ga kujeru ka xauna" Yana kallon drip din da aka sa mata yace "Am comfortable ma" tace "Toh yyi kyau" Mariya ce ta shigo dakin rike da warmer din abinci ta ajiye tace "Bata tashi ba har yanxu?" Mummy tace "Eh bata tashi ba" Mariya na kallon Mujaheed tayi murmushi tace "Ina yini Dr?" Mujaheed ya mayar mata murmushin yace "Lafiya lau Mariya" Mummy na kallonsa tace "Kai ma likitan ne kenan" shafa kai kawai yyi yana murmushi, Mariya tace "Ehh Dr ne, a Chasel hospital yake aiki" Mummy tace "Maa sha Allah, that's good" Shi dai Mujaheed bai ce komai ba, Sadeeq dai sai danna wayarsa yake babu yabo bbu fallasa, Mujaheed ya kalli agogo yace "Xan je in yi isha, xuwa anjima xan dawo in sha Allah" Mummy tace "Toh sai ka dawo" daga haka ya nufi kofa ya fita, Mummy na kallon Sadeeq tace "Are they of the same mother?" Girgixa kai Sadeeq yyi har sannan yana danna waya, Mummy tace "Stepmother dinta ce warce ta fita yanxu?" Sadeeq ya kalleta yayi d'an murmushi yace "Not at all, mum din shi wanda ya fita ynxu ne" Mummy bata kuma cewa komai ba. Karfe takwas da rabi Imaan ta farka daga baccin da take, har sannan Mummy na xaune kusa da ita tare da Suhaila sai sadeeq dake xaune idonsa a kan wayarsa, Aunty kuma na can gun Aisha Kanwar sadeeq dake kwance daya ward din, Mummy na kallonta tace "Sannu, ya jikin?" Ta d'an yi murmushi tace "Na ji sauki" Mummy tace "Toh Allah ya sauwake" Shi dai Sadeeq kallonta kawai yake, ta mike xaune a hankali tace "I want to use the restroom" Mikewa Sadeeq yyi ya cire tube din ruwan ta sakko daga saman gadon tana dafa gado sbda jirin da ta ke ji, Mummy dai sai sannu take mata, Suhaila xata kama hannunta tayi murmushi tace "Xan iya" daga haka ta wuce bathroom dake ward din tana dingishi, Mummy dai ta bi ta da kallo, Da alwala ta fito bathroom din ta karasa kan gado ta dau Hijab dinta dake linke, Mummy tace "Sllh xa ki yi?" Imaan ta gyada mata kai, Mummy ta kalli Suhaila tace "Ki tafi can ward din ki dauko darduma" Mikewa Suhaila tayi ta fita, shi dai Sadeeq sai kallon Imaan yake, ita kuwa bata yarda ta kallesa ba, Mummy ta nuna mata kujera tace "Toh xauna kafin ta dawo" ba musu ta xauna saman kujeran, ba a dau lkci ba Suhaila ta dawo da pray mat ta shimfida mata. Imaan na xaune pray mat din bayan ta idar da sllh, Mummy ta bude warmer ta debi hadadden jollof rice da Mariya ta kawo daga gida ta sa mata da enough meat, Mummy tana kallonta tace "Toh tashi ki hau saman gado ki ci abincin" Mikewa Imaan tayi ta hau saman gadon ta mika mata abincin ta amsa a hankali tace "Nagode" Suhaila tace "A hada maki shayi?" Girgixa kai Imaan tayi tace "Wannan ya isheni" Bude kofar ward din aka yi Abba ya shigo da sallama tare da Maimoon, Sadeeq ya mike har ya iso cikin dakin Abba yayi ma Mummy sannu ta amsa tace "Sannu da xuwa" gaishesa Sadeeq yyi Abba ya amsa da fara'a yana tambayarsa mai jiki, sannan ya kalli Imaan dake kallonsa yace "Sannu Mamana, how are you feeling now" tana murmushi tace "Na ji sauki Abba, Ina yini" yace "Lafiya lau, Allah ya kara lafiya daughter" Mummy tace "Ina yini Alhaji" Abba yace "lafiya lau, ya masu jiki" tace "Alhmdllh da sauki sosai" yace "To madallah, Allah ya basu lafiya, Allah kuma ya bada lada" Mummy tace "Ameen" Maimoon ta ajiye ledan fruits dake hannunta tana kallon Imaan tace "Sannu" Murmushi imaan tayi mata, Abba yyi ma Mummy sallama yace xai shiga ya duba sis din Sadeeq, Mummy tace "Tou mun gode Alhaji" yana kallon Imaan yace "Sai da safe Mamana, Allah ya kara lafiya" ta amsa da "Ameen, thanks Abba" tare suka fita da Sadeeq da xai kai sa gun sis dinsa. Basu kai minti biyar da fita ba Mujaheed ya shigo dakin hannunsa rike da leda, Tun da suka hada ido Imaan ta sunkuyar da kanta, ya karaso ciki yana ma Mummy sannu, Mummy tace "Har ka dawo" yace "Ehh na dawo" Yana kallon Imaan da taki yarda ta kallesa yace "How are feeling now" still bata kallesa ba tace "Na ji sauki" ya ajiye ledan hannunsa a table, yana silencing wayarsa dake ringing, Mummy ta nuna masa kujera tace "Toh ka xauna koh" ya d'an yi murmushi ya xauna saman kujeran, Imaan dai sai juya abincin gabanta take, Mummy tace "Ba fa cin abincin kike ba" diba tayi ta kai baki ta dago kai tana kallon Mujaheed dake kallonta, a hankali ta dauke kanta tana cin abincin. Sai kusan karfe goma Sadeeq ya dawo dakin, Tun da ya kalli Mujaheed sau daya ya dauke kai yana kallon Mummy yace "Xa a mayar da ke gida ne tunda Suhaila da sis dinta na nan?" Mummy tace "Don't worry nan da anjima sai in tafi" Yace "Ohk" karasawa yyi kusa da Imaan murya can kasa yace "Ba inda ke maki ciwo ko?" Ta gyada masa kai kawai, yace "Ohk, xan je gida in dawo yanxu, I want to freshen up" ta kallesa tace "Ohk" murmushi ya sakar mata ta sunkuyar da kanta, ya juya yana kallon Mummy yace "Xan dawo ltr mum" daga haka ya nufi kofa Mummy tace "Toh ai ba ku yi sallama da Dr ba" Juyowa sadeeq yyi ya kalli Mujaheed yace "Ohh I didn't notice him, see ya ltr..." Mujaheed ya d'an yi murmushi yace "Alright" Daga haka ya fice daga ward din. Imaan ta daga kai ta kalli Mujaheed taga kallonta yake ta turo baki ta dauke kai, Mujaheed bai bar hospital din ba duk da kiran da Safeenah da Umma suka dinga lafta masa, ya kuma ki dagawa, har sai da Umma ta kira Maimoon tace ta kai masa waya, Maimoon na kallonsa ta mika masa wayar tace "Ya M.A...." amsan wayar yyi ya kai kunne, cike da bala'i da masifa Umma tace "Mujaheed wai Kanwar Uwarka ko ta ubanka ce kwance gadon asibiti???" Shi dai bai ce mata komai ba, rai bace tace "Tun raina bai gama baci gaba daya ba ka kama hanyar gidan ka yanxun nan, ka bar yar mutane can ita kadai tsakar dare kamar ni ce kwance ba lafiya a gadon asibiti, ko meye hadin ka da sauran ciwon?" Mujaheed bai ce komai ba ya katse wayar ya mika ma Maimoon ta amsa, Mujaheed bai bar asibitin ba duk da fadan Umma sai kusan Sha daya da wani abu, shi ma Mummy ce tace masa amma ba shi da family, Bai bata amsa ba sai murmushi da yyi ya mike yace "Toh sai da safe, Allah ya bada lada" tace "Ameen" Imaan dake kwance ta rufe ido kamar mai bacci, ta bude idon ta bi sa da kallo har ya isa kofa, sai kuma ya juya ya kalleta, da sauri ta rufe idon, har xai fita sai kuma a hankali tace "Sai da safe" Yana kallonta yace "Allah ya tashe mu lafiya" daga haka ya fita ya rufe kofar. Washegari aka sallami Imaan karfe sha daya na safe, Stepmum din Sadeeq da su Suhaila ne suka kai ta har gida, Ammi tayi masu godiya tare da Aunty, basu wani jima a gidan ba suka wuce tunda tare suke da driver. Bayan sati daya da yayi dai dai da saura sati guda a kawo lefen Imaan.... Umma ce xaune makeken parlon gidan Bulasawa tare da Hajiya Balaraba sai Safeenah da ta ke ta taunan cingam ta ci kwalliya iya kwalliya tayi kyau, ba don Suhaila da ta gansu bakin gate a tsaye ta dawo boko a motarta ba da babu yanda xa ayi a barsu su shigo gidan don masu gadi sun ce ba a sanar da su xa ayi bak'i ba, ynxun ma sun fi minti sha biyar xaune parlon suna jiran fitowar uwar gidan Bulasawa, duk sun yi shiru kamar masu xaman makoki, can dai Hajiya Saude na kallon Umma murya can kasa tace "Anya shawarar nan tayi kuwa Hajiya Rukayya??" Umma na kallon Safeenah tace "Ni ban kawo hakan a kai ba fa, sai da Safeenah ta kawo shawarar, kuma jikina ya bani da nasara...." Safeenah ta tabe baki tace "Ku dai ba ni nace ayi haka ba?? ku kwantar da hankalin ku kawai, na fa san abinda nake, haka kawai ga hanya mafi sauki kuyi ta kai ma katti kudin ku suna cinyewa, har yanxu ban ga alamar abun da ake ta ce maku ba gashi saura sati a kai lefe a sa rana, ga dai hanya straight...." Umma tace "A'a wllh babu me cinye min kudi, ana biya min bukatata yanda ya kamata... So nawa kuma??" Shigowar Mummy parlon sanye da hijab har kasa yasa duk suka yi tsit, kallonsu ta dinga yi har ta karaso ta xauna saman kujera, Umma na murmushi tace "Sannu da fitowa Hajiya" Mummy tace "Yauwa daga Ina?" Umma tayi yar dariya tace "Lahh, baki gane ni ba Hajiya??" Mummy dai sai kallonta take don sarai ta gane ta, can kuma ta girgixa kai tace "A'a ni ban gane ku ba, daga Ina?" Umma tace "Toh ni dai sunana Hajiya Rukaiya, in dai kina jin Barrister Ahmad Yusuf na nan kaduna to Mai gidana ne..." Mummy bata daina kallonta ba tace "Ohk..." Umma tayi kasa da murya tace "Hajiya a matsayina na yar uwar ki musulma na xo maki taimako albarkacin musulunci..." Da mamaki Mummy tace "Taimako kuma? Wani irin taimako nace maki ina bukata??" Umma ta gyara xama tace "Hajiya don nace na xo maki taimako ba ina nufin kudi ko wani abu gareni da xan baki ba don kin fi karfinsu, amma ki sani wllh wllh taimakon nan sai ya fi maki kudi ko wani abu na kyale kyalen rayuwa... Hajiya kin san shi aure ba abu bane da xa ayi na rana daya a gama ko na wata daya, A'a rayuwa ce da ake fata ya xama na har abada, kin ga wannan yarinyar da d'an ki ke nema??" Ita dai Mummy kallonta kawai take, Umma tace "Toh wllh wllh kin ji rantsuwar musulmi sickler ce, sannan kin ga yanda kika ganta ita kadai, to har gun iyayenta ita kenan takk... uwar ta fi shekara 13 bata haihu ba, kafin daga karshe taje ta san abinda ta yi Allah ya bata yar, wanda da Allah ya tashi kamata ya hadata da sickler, har yau kuma wllh tllh uwar ta hana uban karin aure kiri kiri, sannan babu wanda bai san abinda take ba, daga ita sai yar suke yanda suka ga dama a daulan uban, matar kanin mijina ne uwa daya uba daya, kin ga dai ba kishiyata bace ita balle ace ina ma 'yar ta bakin ciki, ko daya wllh ba haka nake ba, gaskiya ce duk inda take sai na fade ta, yanxu haka maganar da nake maki d'an kishiyata Yusuf ni ce kan gaba gun nema masa aure gidan Alhaji Mukhtar Kiyawa da kika sani dai na nan garin, wllh wlh mahaifiyar yarinyar nan ba mutuniyar kirki bace muguwar bafillatana ce ta karshe, kije anguwar mu malali ki shiga gidajen layinmu kaf kiyi tambaya a kanta xa ki sha labari, tayi kadan in mata hassada wllh balle ace ko hassada nake mata, Bari ki ji Hajiya wllh a ta dalilin ta Mai gidana ya min kishiya, ta cusa masa aminiyarta ina ji Ina gani ta aure min miji, ita kuma taki barin a mata kishiyar har yau gashi ba haihuwa take ba, ita ma kuma ita kenan gun uwarta, sae gashi ta haifi kwaya daya ita ma, kakar yarinyar ma gwaggwo ita kadae iyayen suka haifa aka ce, kamar yanda baxan so Mujaheed da abinda xai cutar da shi a rayuwa ya xame masa wahala ba haka baxan so ma duk wani matashi ko da ba ni na haifesa ba, a wata wllh uban yarinyar na kashe mata kudi ya fi dubu dari biyu, kullum cikin abu daya ake idan ciwon ya matsa mata kuwa ke kya ce baxata yi ba, shi sa nayo tattaki in sanar maki ki ceci d'an ki, barin ma shi da yake d'an ki na fari....." *Imaan isn't for free* it's 300 via Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah Then u show ur evidence of payment via my WhatsApp number 07087865788Umma tayi shiru tana kallon Mummy tana jiran jin abinda xata ce, sai dai fa gabanta faduwa yake, Safeenah da Hajiya Saude ma kallonta suke su ji abinda xata ce, Mummy da tayi shirun kusan minti biyu ta sauke ajiyar xuciya daga karshe tace "Alright, I will look into the matter, nagode da shawara" Umma tace "Atoh, banda mai sonka wa xai kawo maka haka har gida, yanxu xamani ya lalace mutane basu son fadin gaskiya ga ta nan dai kiri kiri ana ganinta, wllh bbu wanda bai san abubuwan nan da na gaya maki ba amma sai mutune su yi gumm su xuba ido, to mu ba mu gaji haka a xuri'ar mu ba gaskiya" Hajiya Saude tace "Wllh ko a gaban uwar yarinyar ce xa mu iya fadin abinda Hajiya Rukayya ta fada maki a nan tunda ba tsoronta mu ke ba, gaskiya ne dai sai mun fada, sam matar bata da hali, makirace ba ta wasa ba, yanxu haka ita gani take ta ci nasara tunda bbu wanda ya isa ya fito ya fadi aibunta duk ta rufe bakin kowa...." Mummy tace "Na ce maku xan yi shawara ai koh?" Umma tace "Toh Allah ya baki ikon yin wanda baxa ki dawo kina da kin sani ba wataran, Allah kuma nuna maki duk abubuwan da muke fada da idon ki, kai ko spy mace ne xa ki iya biya ta dinga shigowa gidan namu taga wainar da ake toyawa, wllh wllh duk ta mallake gidan......" Daga haka ta mike tana murmushi tace "Nagode da lkcn da kika bani Hajiya, Allah ubangiji ya mana xabi nagari..." Tana nuna Safeenah tace "Yar wajen Hon Usman Basiru ce wannan... Kuma surkata ce d'ana na fari ke aurenta, yanxu haka sun kusa wata uku da aure" Mummy na kallon Safeenah tace "Maa sha Allah, that's nyc, Allah ya bada xaman lafiya" Safeenah ta mike tana amsawa da Ameen, Hajiya Saude ma ta mike nan suka yi ma Mummy sallama, Mummy tace "Toh nagode, sai anjima" Umma tace "Mu jima da yawa Hajiya" kofa suka nufa kafin su isa kofar Sadeeq ya shigo parlon, kallon Umma ya dinga yi da mugun mamaki da su Safeenah, Umma ta sunkuyar da kai ta fita parlon su Hajiya Saude na biye da ita, Sadeeq na kallon Mummy ya karasa cikin parlon ya xauna har sannan fuskarsa na dauke da surprise yace "Mum what is she here for??" Mummy tace "It's not necessary you know Sadeeq" ya mike cike da damuwa yace "Why will u say so mum, don Allah ki gaya min me ta xo yi?" Mummy ta mike tace "Nace maka it's not necessary Sadeeq, I am busy upstairs pls" daga haka ta wuce ya bi ta da kallo, a hankali ya koma kan kujera ya xauna ya jinginar da kansa jikin kujeran ya rufe ido xuciyarsa na bugawa. Bayan kwana biyu Sadeeq ya shigo part din mum dinsa ya ganta da sisters dinta da few frnds a parlor suna xuba lafiyayyu kuma tsadaddun kayan lefen da aka yo daga Dubai cikin boxes set shidda sau biyu, sosai boxes din suka yi kyau sannan they look sooo unique kana gani kasan ba da kudin wasa aka siye su ba, Mummy na kallonsa tace "Perfumes da kace xaka Karo fa??" Yana dai tsaye yace "Ohk suna wajen Aunty" ta masa wani kallo tace "Wajen Aunty Kuma?? Me ya kai su can?" Shiru yyi bai ce komai ba, Kawar Mummy Hajiya Farida tace "Toh Aunty ce ta nemo maka mata da xaka bata kudin siyan turarurruka, kai sai samm baka san ciwon kanka ba Sadeeq, kila ma har ka hada yarinyar da ita Auntyn koh?? tunda ga kanwar uwarka" Shi dai bai ce komai ba, ya juya ya fita, Mummy ta bi sa da harara, Hajiya Farida tace "Ni fa ban ji dadin da tasan yarinyar tun a asibiti ba wllh, Bai kamata ta san komai ba a maganar auren nan" Imaan na xaune dinning misalin karfe sha daya na safiyar lahadi tana answering past questions din gabanta kasancewar gobe xa su fara waec, aka bude kofar parlor.... Inna ce ta shigo parlon da sallama Imaan na kallonta har ta karaso ciki tana tabe baki murya can kasa tace "Ko turaren wuta bana jin an sa ma parlon nan yau, dama fa tsafta sai wanda Allah ya so da Rahama yake ba ma, mu dai mun gode masa....." Imaan tace "Toh ba sai ki sa mana ba tunda ba mu sa ba" da sauri Inna ta juya ta kalleta, Bata dai ce komai ba ta xauna saman kujera, Imaan ta ajiye pen din hannunta ta shigo parlon tace "Ina xa ki je da sassafe haka?" Inna tace "Ina xan je kuwa da ya wuce gidan Mujaheed, wa gare ni banda Allah sai shi, jiya fa haka ya xo bashi da isasshen lafiya duk ya rame sai 'yan idanuwa, ya xama wani tsololo da shi sai tsayi kamar pal waya, ni dai ba ruwana wllh, Mujaheed da ko ciwon kai da kyar ka ji yana yi sai gashi duk ya xabge haka kamar ana cin namansa, ni ko nace anya matar nan ba mayya bace aka lika masa ya aura kuwa?? Tun fa da aka yi auren yake a haka yau lafiya gobe babu, toh ni dai yanxu gidan xan tafi idan ma Safara'u mayya ce muna hada ido xan gane, mayu kuma wasu iri ne ba mu kara da su ba a duniya, Ni wllh har dambe nayi da mayya, kuma da kyar idan Safara'u ba mayya bace" Imaan dake kallonta da mamaki tace "Mayya kuma Inna" Inna tace "Oh oh Allah, to idan ba mayya bace mecece, ce min yayi fa bai san me ke damunsa ba da na tsare sa jiya, wllh da barbajin gaskiya a xancena, ni dai duk abinda ya samu Mujaheed ni ya sama kuma baxan xuba ido haka ba, a kan Mujaheed sai duk in tada gidan nan Al-quran, ni bai fiye min kowa sau dubu dari biyar ba aka ce maki, idan xa ki tafi ki shirya ki tafi ki shirya mu tafi gidan yanxu in san abun yi, dama kuma ki taho da takadda da biro duk yanda muka yi da shegiyar matar xa ki rubuta min, don tambayoyi xan mata na dangin uwa da uba, a nan xa a gano tushen abun...." Xaunawa imaan tayi tana kyalkyala dariya sosai, Inna ta wani hade rai tana kallonta tace "Amma ke kam baki da da'a, Meye abun dariya a nan jikana na can rai a hannun Allah, Toh ni fa wllh a kan Mujaheed sai ince a fasa kawo kayanki da sadaki yau ba ruwana, haka kawai jikana ba lafiya xa a cika ma mutane gida da jama'ah... Bari ma in je in sami Ahmadu yanxu tunda ke matar banxa ce baki da mutunci" wani kallo Imaan tayi mata tace "Toh ni ce bani da lafiya da xa a fasa kawo kaya???" Inna ta saki baki tana kallonta, can ta mike tana kwalo ma Ammi kira, Ammi ta fito da sauri tana amsawa, rai bace Inna na nuna mata Imaan tace "Wllh jaraba kika haifa Aisha, mu dai kaf danginmu babu butulu wllh ban dai san ya naku yake ba, gaskiya imaan butulu ce, banda haka kiri kiri ta fito ta nuna ciwon d'an uwanta bai dameta ba saboda tana 6arin jiki tayi aure, baki ta6a xaunar da ita kin bata labarin irin bakar wuyar da Mujaheed ya sha da ita tun tana tsummarta bane wai? Ni dai wllh a dinga jin tsoron Allah, wllh baki xaunar da ita kin sanar mata ba da baxata fifita aure kan d'an uwanta na jini ba, idan ban sa an fasa kawo kaya ba gidan nan yau a kan Mujaheed ace ba ni bace, lefen banxa da hofi jikana ya fi lefe ne, wllh jiya baccin kirki ban yi ba sai da safe bacci ya kwashe ni, ban tashi ba sai daxu na shirya a gurguje na taho ta raka ni gidansa in ga abinda yake ciki, nace to ko ma matar ce mayya xan je in ga" Imaan ta tabe baki tace "Ba fa inda xan je gobe Ina da jarabawa, ko kuma ni likita ce da xan biki...." Inna ta fashe da kuka ta nufi kofa tace "Eh lallai Imaan ta xama jarabar duniya, Bukar ya haifi jaraba, Allah ka mana iyaka da Butulu duk inda yake.... Bari naje in samu Ahmadu ai na fi ki tsiya yau" daga haka ta fice daga parlon, Imaan na turo baki ta juya xata koma dinning Ammi tace "Wuce ki shirya ki bi ta ku tafi" ta juyo da sauri kamar xata yi kuka tace "Ammi karatu fa nake, ni wllh bana son xuwa gidan Yaya..." Ammi ta hade rai tace "Musu xa ki tsaya yi da ni kenan?" Lkci daya hawaye ya kawo idonta ta wuce dakinta, atamfa riga da skirt ta fiddo ta saka bayan ta feshe jikinta da turare, ta goga chappete a bakinta ta sa gogaggen Hijab dinta har kasa ta fito parlor rike da wayarta da karamin jaka, Ammi dake xaune parlor ta bi ta da ido, a hankali tace "Ammi sai mun dawo" Ammi tace "Allah ya kiyaye, you pray before leaving" Imaan ta gyada mata kai ta nufi bakin kofa tana karanto addu'ar fita gida a ranta. Part din su Maimoon ta nufa ta bude parlon ta shiga a hankali, ko karasawa cikin parlon bata yi ba ta dinga jin Muryar Inna a parlon Abba tana cewa "Gaba daya Imaan ta banu ta lalace, sam bata da kirki yanxu, amma abinda ya ban tsoro shine yanda aka boye mata wuyar da Mujaheed ya sha a kanta, bata fa yarda da kowa a lkcn sai shi sai uwar, duk ta fitsare masa jiki, har uban nata Bukar tsoron sa take... Toh meye kuma lkci daya sai yarinya ta xama jarababba mara Imani, ni ka ma kira min Bukar din in ji ko su ke koya mata, dariya fa ta dinga ba66akawa daga nace mata Mujaheed ba lafiya xan je gidansa, ni wllh na gaji da imaan a gidan nan" shi dai Abba bai ce komai ba kansa na kasa yana sauraranta, ta tabe baki tace "Ni dai ba ruwana, shi kuma Mujaheed gaskiya sai mun tashi tsaye kansa don idan aka rasa sa ni nayi asara ba wani ba, idan ma auren ne bai so gaskiya sai a raba yau yau din nan, ba ruwana a kai ni a baro in shiga uku" Sai a sannan Abba ya kalleta yace "Xaxxabi fa kawai yake, amma ai yana jin sauki yanxu..." Tsaki Inna ta ja tace "Tunda ba jikin ka bane ba dole kace yana jin sauki ba Ahmadu, gansamemen mutumi da ya dinga min rawan sanyi jiya sai da na rufa sa da katon bargo shine xaka ce yana jin sauki, ku dai ku dinga jin tsoron Allah, wlh ku ji tsoron Allah, tunda ba wani ya min wahala da shi ba to ni xan je yanxu inji abinda yake ciki, idan ma matar ce mayya duk xan gani" Da mamaki Abba yace "Subhanallah, haba Inna ya kike irin wannan magana haka, wannan fa babban magana ne ka ce ma mutum maye...." A fusace Inna tace "Na ce mata mayyar, idan ba mayyar bace ina dawowa ai xan ce ba mayya bace, tsoron ubanwa aka ce maka xan ji banda Allah, shi kadai ne abun tsoro dama, kuma ni da shi nayi imaani" dai dai shigowar imaan parlon, kanta a kasa ta gaida Abba, Abba ya amsa yana tambayarta jiki domin jiya yini tayi ciwon kafa, Inna tace "Ya jiki?? Ce maka aka yi bata da lafiya, Ga dai bawan Allah me ciwo can a kwance xaka tambayi lafiyayyar mata ya jiki" tana fadin haka ta tabe baki ta mike tace "Toh yanxu xa ka kirasu ka sanar masu d'an ka na fari ba lafiya a bar kawo lefen da kudin aure sai wani satin koko?" Da sauri Imaan ta kalleta, Abba yace "Haba Inna, ae wannan bai shafi ciwon Mujaheed ba, Ina ruwansu da wannan, shi Mujaheed din yaro ne, don Allah ki yi hakuri ki bar xancen nan Inna bai ma kamata ba, ga yanda dai muka yi da mutane kuma ki kawo wata magana daban" Inna tace "Atoh ni dai duk abinda ya sami jikana Allah ya isa wllh...." Daga haka ta fice daga parlon a fusace, Imaan tace "Abba sai mun dawo" ya gyada mata kai kawai ta bi bayan Inna, har suka isa titi Inna bala'i take idan abu ya sami Mujaheed ya sami kowa, ita dai Imaan sai turo baki take tana tsaye gefenta, Inna ta tsayar da adaidaita ta shige yana tambayarta inda xata a fusace tace "Don Allah ka rufa min asiri yaro ka ja mashin dinka mu je, meye kuma Ina xanje kamar yar yarinya, jikana ne fa ba lafiya rai a hannun Allah gidansa na can unguwar dosa ana ma kyautata xaton matar ce mayya, kuma kana ta cewa ina xan je" Mai adaidaitan bai tanka ta ba, Imaan ta hade rai ta shige adaidaitan. Har suka isa gidan Mujaheed mita take ita kadai daga imaan har mai napep babu mai ce mata komai, suna sauka kafin ta fiddo hamsin ta mika masa Imaan ta basa dari biyar din hannunta don bata ma son dogon xance, ya ciro dari biyu ya mika mata, Inna ta saki salati tace "Nawa ka cire bawan Allah?" Imaan tace "Toh ai ba kudin ki bane Inna, kayi wucewan ka kawai" Mai adaidaitan ya ja napep dinsa yyi gaba Inna ta dinga jaraba tana kiransa barawo tuni imaan ta shige cikin gidan ta bar ta tsaye a bakin gate, dai dai balcony ta tsaya ta rungume hannu tana jiran shigowarta, Can sai ga ta ta shigo compound din tana cewa "Babu abinda kudin Bukar xai masa a rayuwar nan ta duniya, iyaka ma ya gudu ne da wahala da Bala'i tunda bamu basa ba" bata ko kalli Imaan ba ta murda kofar parlon ta bude ta shiga, Imaan ta turo baki ta bi bayanta, Umma ce ta leko daga kitchen tana soya kwai da dankali, Inna ta rike ha6a tana kallonta a hankali tace "Wacece wannan?" Umma dake sanye da hijab har kasa ta gaisheta a dakile ta koma kitchen din, Safeenah ce ta sakko parlor sanye da doguwar riga na material hannunta rike da tray na cup, ganin Inna ta dauke kai ta hade rai hade da tabe baki tace "Sannu da xuwa" Inna tace "Ina Mujaheed din???" Safeenah tace "Yana sama an sa masa drip" Inna tace "Ai ni na shiga uku, abun har ya kai an fara sa drif... Toh aniyar kowa xai bi sa wllh babu abinda xai sami jikana" Kallon Imaan tayi tace "Ke mu je in gansa..." Imaan ta nufeta, da sauri Safeenah tace "Inna a can dakinsa yake fa...." Inna ta juya tana kallonta tace "Dakinsa kuma? Toh da ina nace maki xan je banda dakin nasa? Ko nace maki dakin ki xan shiga Safara'u?" Safeenah tace "A'a da naji kince ku tafi, idan ma tafiyar ne ke da kike matsayin kakarsa ai sai ki tafi dakin" Inna ta gyara tsayuwa tace "Toh ita Imaan din fa??" Safeenah ta d'an hade rai tace "Wannan ba hurumin ta bane gaskiya shiga dakin mijina, bata da wannan hurumin, dakinsa sirrina ne da nashi" Salati Inna ta xabga ta xauna kan kujera tayi tagumi tace "Naga abinda ya isheni ni Asabe... Safara'u kinsan me kike cewa kuwa, wani sirrin ku ke da shi ke da Mujaheed da ba mu sani ba, kinsan wacece kike kokarin hana shiga dakin nasa kuwa???" Umma ta fito kitchen bbu yabo bbu fallasa tace "A'a inna, xancen gaskiya ayi ta, dakinta ne da na mijinta fa kuma kice wata daban ta shigar masu, a kan wani dalilin?? sai kace dai a garin ga6a ga6a muka taso, ko a musulunce ai hakan haramun ne ma wata ta shigar maki turakan miji..." *Imaan isn't for free* it's 300 via Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah Then u show ur evidence of payment via my WhatsApp number 07087865788Mikewa Inna tayi ta bude baki tana kallon Umma tace "Rukayya ita imaan din ce wata a gidan Mujaheed?? Ita Imaan din?? Ehh lallai ba shakka kin xama mahaukaciya, to wllh tllh Imaan ta fiye ma Mujaheed Safara'u sau dubu dari, wacece kuma Safara'u Allah na tuba?? Sannan yaushe kika san Allah da kike kokarin min wa'azi wai kar ta shiga daki ta duba yayanta? Toh kwanciya tace maki xata yi a dakin idan ta je?? Ko ko ce maki tayi bata da kwakkwaro kamar ki ne?? Ni dai na ga abinda ya isheni, ba kunya ba tsoron Allah kin kwaso jiki xalalo xalalo kin xo gidan surka kina girki a kitchen ita kuma tana sama wajen miji, anya Rukayya?? A'a tunda uwata ta haifeni ban taba gani ko jin haka ba wllh, Toh ni duk ba wannan ba, don bai dameni ba... Babban magana a nan shine gaskiya ban gane kan ciwon jikana ba, don wannan ciwo ba na Allah bane, tunda ya auri wannan mata Safara'u yayi bankwana da lafiya, yau ciwo gobe lafiya, yau fari gobe tsumma, To a kan me? Ita Safara'un yar wace gari ce in ji tukun kafin in san abun yi" Umma ta dinga mata wani kallo tana jin kamar ta tanka ta amma wata xuciyar na bata hakuri, fuska daure Safeenah tayi wucewarta kitchen tana kas kas da cingam ta bar su nan tsaye, Inna ta gyada kai tace "Toh kya ci uban ki kuwa ba dai jikana ba don kurwarsa daci ne da ita yarinya, in sha Allahu sai dai ki ci uwarsa da ta jajibo ki ba shi ba, kuma xaman ki saura kiris a gidan nan" daga haka ta ja hannun Imaan dake tsaye gefenta suka wuce sama tana huci, Umma ta bi su da wani kallo xuciyarta na tafarfasa tasan dai ko hauka take baxata tanka Inna ba, Inna ta bude kofar parlon dake sama ta shiga, Ganin Imaan ta ki shigowa ta fixgota a fusace ta nufi dakin Mujaheed da ita, Imaan dai sai bin ta take, kwance Mujaheed yake saman gado idonsa rufe, Inna na kallon empty robber din drip dake sakale ta rike ha6a tace "Ka ji jarababbu mayu, wai an sa masa ruwa yana daki, alhalin ga ruwa ya kare..." Bude ido Mujaheed yyi, Inna ta fashe da kuka a hankali ta nufesa tace "Sannu Mujaheed, in sha Allahu babu abinda xai sameka in dai ina da rai, asiri dai ya gama tonuwa na gano komai" shi dai gaba daya hankalinsa na kan Imaan da tayi tsaye bakin kofa ta ki shigowa kuma ta ki yarda su hada ido sai wasa da fingers dinta take, Inna ta xauna gefen gadon tana goge guntun hawayen idonta tace "Kwana nawa da aurenta ka fara jin canji a jikin ka??" Shi dai bai ce mata komai ba har sannan yana kallon imaan, Inna ta juya ta kalleta tace "Ke dai baki da kirki wllh, halin ki abun tsoro ne gaskiya, baxa ki karaso ki gaida sa ba" sai a sannan imaan ta kalli Mujaheed, suna hada ido tayi saurin dauke kai ta karasa cikin dakin ta duka kasa kusa da gadon a hankali tace "Ya jikin Yaya?" Bai tanka ta ba, Inna tace "Atoh, abinda ma da kyar ta biyoni Mujaheed, wllh Imaan bata da imaani, har fa ce min tayi toh ita ce bata da lafiya da xance a fasa kawo kayan aurenta yau sai wani satin sabida baka da lafiya...." Mujaheed dai ya kasa daina kallonta, imaan ta wani hade rai tana kallon Inna, bude kofar dakin aka yi sai ga Safeenah ta shigo da warmer a rufe da plate a hannunta, ko kallonsu bata yi ba ta karasa ciki ta ajiye ta xauna kusa da kansa tana wani yauki tace "Baby ka tashi ka ci ko kadan ne sai ka sha drugs dinka plss, bacci ma ya kamata kayi ka huta bayan ka gama cin abincin tunda sai ltr xa a sa wani drip din" Imaan ta dinga hararanta ta gefen ido, Inna ta tsuke fuska ta rungume hannu tana karanto addu'a a xuciyarta tana tofawa a duk angles din dakin, Mujaheed ya mike xaune ya cire duvet din jikinsa yana kallon Safeenah yace "You don't worry anjima xan ci, na sha tea yanxu" tace "Toh ayi maka pepper soup din ko appetite dinka xae dawo?" Da kamar baxai ce mata komai ba sai kuma yace "Ohk" Ta mike tana wani cat walking ta nufi kofar fita tana karkada jiki, Imaan ta wani tabe baki ta dauke kai fuska daure, Safeenah na fita Inna ta mike ta dau abincin ta bude window ta xaxxage gaba daya downstairs ta juyo tana kallon Mujaheed murya can kasa tace "Mayya ce Mujaheed...." Bude baki yayi yana kallonta da mamaki, ta kyabe baki ta cire Hijab dinta ta linke tace "Jira in je in soya maka wani gaskiya, Allah ba batun wasa ba an gano mayya ce amma kada kace mata komai tukun, a hankali ake kama barawo, anjima ta Rasulu tace min xata xo nan....." Bai san lkcn da yyi murmushi ba bai dai ce mata komai ba, kofa Inna ta nufa fuska daure ta fita xata kitchen ta masa girki, Imaan na ganin haka ta mike da sauri ta nufi kofa yace "Fatima" tsayawa tayi sai dai bata juyo ba, jin bai ce komai ba a hankali ta juyo tana kallonsa, taga kallonta yake, sosai gabanta ya fadi, kamar xata yi kuka tace "Na'am" jin yyi shiru ta karasa kusa da gadon ta durkusa tace "Ga ni" ya sauke idonsa daga kallonta yace "Ya preparation na exams?" A hankali tace "Lafiya lau, how are you feeling now?" Yana kallonta yace "Dama kin san bani da lafiya ashe?" Tace "Aa ni Inna ce ta gaya min daxu Allah ban sani ba" Bai ce komai ba hakan yasa tace "Xan je in taya Inna" yace "Promise me baxa ki wuce gida ba daga nan" murmushi tayi ta boye fuskarta da gado don abinda ke ranta kenan, ji tayi ya kamo hannunta ta dago da sauri yace "Kar ki tafi yanxu Imaan" ta turo baki tace "Bayan Umma tana nan, kuma matar ka sai wani hararana take yi, ni dai wucewa xan yi" yace "Toh kiyi xamanki a nan" ta xaro ido tace "Kaga Inna ta wuce fa, salon idan matarka ta shigo ta xageni ko" yace "Kina dai son wucewa kawai" tana murmushi tace "Toh naji baxan wuce ba, amma me ke damun ka Yaya? Ji fa ka rame sosai" Ya jinginar da kansa da gado murya can kasa yace "Ban sani ba" ta langwabar da kai tace "Kana likita kuma baka sani ba, or is about our last talk, I mean about the lady..." Shiru yyi yana kallon Ac dake aiki a dakin, murya can kasa yace "Yau xa a kawo kayan ki koh?" Dariya tayi ta boye fuskarta tace "Uhm nima ban sani ba" jin bai ce komai ba ta dago tana kallonsa, kallonta taga yana yi da manyan idanuwansa, ta sunkuyar da kai tana murmushi tace "Ehh yau ne" yace "And u are happy" ta turo baki ta ki cewa komai, sauke kafafuwansa yyi daga saman gadon ya nufi press dinsa ya fiddo gogaggen shirt xai saka a kan singlet da 3 qtr din jikinsa, Bude kofar dakin aka yi sai ga Safeenah, da wani expression ta dinga kallonsa sai kuma ta kalli Imaan a nutse tace "Malama tashi ki fitar min dakin miji, naga alama karuwancin naki ba iya waje ya tsaya ba har gida" Imaan na mata wani kallo tace "Karuwanci kuma? To sai dai in kece karuwa....." Bata rufe baki ba Safeenah ta sauke mata mari tana wani huci tace "Ni kike ce ma karuwa a dakin..." ita ma bata kai karshe ba taji saukan wani wawan mari da yasa ta ji dumm a kunnenta, da kyar ta juya tana ganin stars ta kallesa cikin rawar murya tace "Mujaheed. .." ya kuma wanke ta da wani mahaukacin marin ya fixgota yana huci yace "Kinsan warce kika mara Safeenah??" Safeenah ta xaro ido a tsorace tana kallonsa, sai kuma ta rushe da kuka cikin tashin hankali tace "Yanxu a kan wannan matsiyaciyar ka mareni Mujaheed, a kan wannan sauran ciwon....." Hankada ta yyi iya karfinsa don har sai da ta fadi kasa timm, Yana nuna ta calmly yace "Kece matsiyaciya ba ita ba" Safeenah ta mike da sauri ta fice dakin da gudu tana kuka, Imaan da hankalinta yyi mugun tashi tana kallonsa cikin rawan murya tace "Yaya me yasa ka mareta, ai xan iya ramawa da kai na, why did you slap her, you shouldn't have, beside umma fa na gidan" Mujaheed ya rikota cikin daga murya yace "Did you know what I felt da ta mare ki imaan?? Kinsan abinda naji?? Me yasa xata daga filthy hand dinta ta daura a fuskarki??" Ta dinga kallonsa da manyan idanuwanta ko kiftawa babu, yyi kasa da murya yana sauke numfashi a hankali yace "Wlh da ni ta mara baxan ko daga kai in kalleta ba, why will she slap you Imaan???" Kallonsa kawai imaan take ganin yanda idanuwansa suka kada sosai, lkci daya ya rungume ta ya lumshe ido, a hankali ta kwantar da kanta kirjinsa tana jin yanda xuciyarsa ke bugawa tana shakan daddadan kamshinsa, gently ya dinga tafiya tana jikinsa har ya isa kofa ya sa makulli. Inna na kitchen tana aikin suyan dankali da kwai, Umma ma na kitchen din fuska daure tana dauraye kayan miya da xa ayi ma Mujaheed pepper soup, lkci lkci take xabga ma Inna harara ta dinga addu'ar da ma man gyadan dake kan gas din ya kware a jikinta kowa ya hutu a duniyar, Inna ta kwashe dankalin karshe a mai tana tabe baki tace "Ba ruwana, ni sai in sa Ahmadu ya tattaro min kayana ma in dawo nan gaba daya, don dai in masa girkin abincin da xai ci ransa kadai kar a cucesa, ni a ma kira min Ahmadun in gaya masa jikin Mujaheed ba sauki masu kawo lefen nan su dakata kawai lefe bai fi jikana ba gaskiya" Umma ta kalleta da sauri, sai kuma tayi kasa da murya tace "Lallai kam, ace duk yanda suke da Imaan baya nan xa a kawo lefe da kudin aurenta, abun bai yi ba gaskiya, daxu daxun nan da safe na gama maganan nan" Inna tace "Atohh, ko tsari babu wllh, Ahmadu ya ki saurarata da yake kunnen kashi garesa, ni bari a kara kiransa in jaddada masa halin da na xo na samu Mujaheed a san abun yi" tana fadin haka ta fice kitchen din, Umma ta kashe gas ta bi bayanta da sauri, jakarta ta dauka ta bude ta dau wayarta ta mika ma umma tace "Kira min Ahmadun" Umma ta nemo lambar Abba ta kira ta sa a hands free ta mika mata, Abba na dagawa Inna tace "Toh wllh Ahmadu Mujaheed na nan rai kwakwai mutu kwakwai, ko magana bai iya yi balle ya ci wani abun, idan xa a ji ta nawa to a dakatar da masu kawo kayan nan xuwa sati mai xuwa, aure bai fi rai ba ku ji tsoron Allah Ahmadu.... Mujaheed rai garesa" Abba dake ta saurarenta yace "Sun kira suna tahowa nan da wani lkci, don haka babu fa'idar fasa komai, sannan ba wai jimawa xa ayi ba balle kice, da sun tafi xa mu taho da Abubakar da likita tunda yaro Mujaheed din ya xama" Inna tace "Toh kuwa kun xama abun tsoro wllh, Allah ya mana tsari da ku" daga haka ta mika ma Umma tace "Kashe min wayata maxa, ni dai ina ganin jarabawan rayuwa" Umma ta katse wayar gaba daya rai ba dadi, don tun safe da ta ji labarin xa a kawo lefen Imaan ta gane xancenta bai yi tasiri ko kadan a gun uwar Sadeeq ba, tun sannan ta kasa xaune sai da ta taho gidan Mujaheed don fada ma Safeenah abinda ake ciki, tana xuwa kuma ta iske Mujaheed kwance wai ba lafiya an sa masa drip, abinda ma ya tsayar da su basu fita ba kenan amma da tuni sun baxama neman duk abinda xai sa a fasa shigo da lefen Imaan gida, a hankali Umma tace "Ba a kyauta ma Mujaheed ba amma gaskiya" Inna tace "Toh wa gareni da xan ma magana ya ji, ai Ahmadu ya dauko hanyar lalacewa shi ma, shi dama Bukar bana sa shi a lissafi kwata kwata" Umma tace "Toh ko xaki ma shi yaron magana, naga kuna shiri sosai" Inna ta mika mata wayar tace "Yauwa duba xa ki ga Bulasawa ki kira, ae yana da fahimta, kawai ce masa xanyi Imaan tace tana jin nauyinsa don Allah in masa magana a dakatar da kawo kayan don yayanta bashi da lafiya yana kwance har da karin ruwa leda uku" Umma ta amshe wayar da sauri tace "Toh hakan ma yyi wllh" tana kiran number Sadeeq ta sa handsfree ta mika ma Inna, Inna ta karbe wayarta ta nufi kofar ta fice parlon gaba daya, Umma ta bi ta da wani kallo tana murmushi, dai dai nan Safeenah ta sakko kasa tana kuka sosai har lkcn tana rike da kuncinta, hankali tashe Umma ta nufeta da sauri tana cewa "Lafiya Safeenah me ya same ki?" Cikin kuka sosai tace "Hajiya a kan wannan shegiyar yarinyar Mujaheed xai sa hannu ya mareni har sau biyu, Mujaheed ya rasa warce xai mara sai ni? Mujaheed slapped me???" Bude baki Umma tayi tana kallonta da mugun mamaki tace "Shi Mujaheed din ya mare ki??" can ta juya ta wuce sama kamar xata tashi sama, Sosai Imaan ta rikice jin muryar Umma tana bubbuga kofar dakin kamar xata cire tana kiran sunan Mujaheed, Lkci daya hawaye ya kawo idonta ta rikosa cikin rawar murya tace "Wayyo Yaya ka gani ko" Xaunar da ita yyi gefen gado ya duka kusa da ita murya can kasa yace "Relax now, ba shigowa xata yi ba na rufe kofar" Inna ce ta shigo parlor tana tabe baki tana kallon wayarta, ganin Safeenah na rusa kuka ta isa kusa da ita ta duka tana kallonta da mamaki, can tace "saboda na xubda girkin da kika masa shine kika xauna nan kina kuka? Ke kya yarda a cuci wani naki??" Bata jira cewarta ba ta wuce sama, tana isa parlon Mujaheed ta dinga kallon Umma dake ta jijjiga kofa, hankali tashe tace "Lafiya?? Makalewa suka yi a ciki??" Umma ta ki cewa komai xuciyarta kamar ya fashe ta huta, da karfi Inna tace "Mujaheed???" Mikewa Mujaheed yyi daga durkushen da yyi gaban imaan da taki kwantar da hankalinta jin muryar Inna ya nufi kofar ya bude a hankali, mari Umma ta sauke masa tana huci tace "ita Safeenahr ka daga hannu ka mara???" Wani salati Inna ta xabga tana kallonta tace "Kina da hankali kuwa Rukayya, Mujaheed din kika mara hka???" Muryar Safeenah suka ji tana cewa "Wllh baxan xauna gidan nan ba yau in har sabida wnn matsiyaciyar Mujaheed ya mareni wllh baxan xauna" Mujaheed ya daga kai yana kallonta fuska daure yace "Ki tafi gidan ku sae na neme ki, kar ki kara ko minti biyar gidana...." Inna tace "Fakat, maxa tattara ina ki ina ki kiyi wucewar ki mayya" gwalo ido Umma tayi tana kallonsa kamar yanda Safeenah ma tayi, cike da karfin hali Umma tace "Safeenar kake cewa ta tafi gidansu Mujaheed??" Bai yarda ya kalleta ba a takaice yace "Ehh Umma ta tafi gidansu" juyawa Safeenah tayi da sauri ta fita parlon, Umma ta kasa cewa komai tana kallonsa with shock can ta juya fuu ta wuce, Inna tace "Tunda kema mayyar ce sabida me baxa ki ji haushin koran Safeenah ba, in sha Allahu xamanta ya xo karshe a gidan Mujaheed...." Shiru Inna tayi tana kallon Imaan ganin hawayen idonta tace "Me aka maki kike kuka?" Kin cewa komai tayi ta juya masu baya, Inna na kallon Mujaheed tace "Kasan yau xa a kawo kayanta da lefe, nace su Ahmadu su jira ka ji sauki ayi komai da kai sun ki saurarata... Yanxu ga dai waya ka Kira min Bulasawa na kirasa daxu ban ji yyi magana ba kila kiran ma bai je ba" Imaan ta juya da sauri tana kallon Inna tace "Me xa ki ce masa??" Inna tace "Wannan ba matsalar ki bace sirri na ne da shi" Mujaheed dai na rike da wayar yana kallonta, ganin haka Inna ta kwace wayarta ta juya ta fita xuwa gun mai gadi don ya kira mata Bulasawa, ganin ana wangale gate din ta tsaya sai ga motar Abba, parking Abba yyi ya fito tare da Daddy da kawu Audu da wani frnd din Daddy daga cikin motar, Inna ta bude baki tace "Kaddai ku ce har sun kawo kayan ni Asabe??" Abba yace "Sun kawo har ma sun tafi, an saka biki nan da wata guda dai dai da lkcn da xa su gama xana jarabawa, sun kuma bada sadakinta dubu dari takwas" Inna tace "Toh da kyar idan Mujaheed xai yafe maku, don wahalan da yyi da ita ku da ku ka haifeta ma baku yi ba, amma sbda butulci ku amshi kudin auren yarinya ba shi sbda cuta ta kamasa?? Toh aji tsoron mutum" daga haka ta juya ta wuce ciki fuska tsuke.... *Maa sha Allah, I will take a break till after sallah in sha Allah, thank everyone for being patient with me all this while following the book Imaan, ayi sllh lfya* *Imaan isn't for free* it's 300 via Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah Then u show ur evidence of payment via my WhatsApp number 07087865788Tun da Inna ta fita parlon Mujaheed ke kallon Imaan dake tsaye ta wani hade rai tana kallon bakin kofa ita a dole Inna ta tafi kiran Sadeeq a fasa kawo kaya, satan kallonsa tayi ganin ynda yake kallonta ta turo baki ta juya xata fita yyi saurin rikota yana kallon eyeballs dinta yace "Don't say anything about what happened between u and my wife to Grandma" kin cewa komai tayi ta kwace hannunta ta fice daga parlon nasa ta sakko downstairs, a nan kuma ta ji shigowarsu Abba compound din gidan da maganganun da suke yi da Inna, Inna ta dawo parlor tana girgixa kai tace "Tunda uwata ta haifeni ban ta6a ganin irin haka ba, su Ahmadu dai sun shiga uku sun lalace tirrrr, yanxu ko Mujaheed kadai bai isa ya karbi auren imaan ba, amma kawai mutane don ba shi da lafiya kuyi masa wannan rashin mutunci, to da kyar idan girman ku bai fadi a idonsa ba gaskiya" Imaan dai sai kallonta take, Inna ta xauna fuska ba annuri tace "Tirrr" Abba yyi sallama bakin kofar parlon ya shigo sannan Daddy da Kawu Audu, Gaishesu Imaan tayi Abba ya amsa yana kallonta yace "Ina Mujaheed din?" Inna ta tabe baki ta dauke kai tana girgixa kafa, Imaan xata wuce sama Abba yace "Ina matar gidan?" Inna ta kallesa da sauri tace "Wace matar gida? Matar gida da ya kora daxu, koko wata daban kake nufi?? ai tuni yace ta wuce gidansu ba wanda bai san mayya bace, daga nan dama ni dai daukansa xan yi mu koma gida ya xauna bangarena ayi ta masa magani har yayi garau" Kawu Audu da ya buda ido sosai yace "Mayya kuma Yaya?" Inna tace "Xancen kake so D'an tsut, tun fa da aka yi auren nan yau lafiya gobe ba lafiya a haka yake kamar mai laulayi, to ina dalili da raina kuma da lafiyata snn ba gantalalliya ba...." Ta kalli Imaan tace "Ke tafi ki kirasa su gane ma idonsu yanda ya koma" Daddy yace "Ni ban fahimci xancen ki ba Inna, ita matar yace ta tafi gidansu ko wa?" Inna na kallon Imaan tace "Ke tafi ki kirasa su gansa bana son dogon surutu da Bukar, don ba hankali isasshe garesa ba wllh, kuma a gaskiya kada Bukar ya sani a bakin duniya ni ba ni na koreta ba da bakinsa yace ta tafi to tunda ba ubanta ya gina masa gidan ba ba dole ta tafi ba, har Rukayya fa a nan na sameta tana masu girki a kitchen daxu..." gaba daya dai sai kallonta suke don har sannan babu wanda xai ce ya fahimci xancenta, Imaan dai ta wuce sama tayi knocking kofar parlor din Mujaheed, sai da ta kara knocking har sau biyu sannan ya bude door din bedroom dinsa, tace "Abba yana kiran ka a kasa" yana gyada kai a hankali yace "You know what Imaan??" Tana kallonsa tace "What??" Yayi wani murmushi yace "I want you to keep this at d back of ur mind... all this ur pretence and everything you are doing... Billah ranan da xan rama yana nan xuwa, I will make u regret all this you are doing in sha Allah" on a serious note ya fadi haka, ta buda ido sosai tana kallonsa da mamaki tace "Pretending kuma? What am I pretending yaya? Ni ban gane ba" yace "Bana son ki gane dama" tabe baki tayi ta juya ta bar wajen ya bi ta da kallo har ta fita sannan yyi wani murmushi. Inna na kallonsu Abba tace "Ni fa ko rantsuwa nayi da kyar inyi kaffara Ahmadu, wai ya xa ku maida ni yarinya da bata san abinda take bane, komai na fada ku karya ta ni ne?? nace maku yarinyar nan mayya ce ita ta kama min jika yake ta ciwace ciwacen da ba na Allah...." Katse ta Daddy yyi ya mike yace "Ke dai Inna ki daina haka, don Allah ki rufa mana asiri ki daina, ni fa gaskiya ba ruwana idan kika jawo wata maganar, ya xa ki dinga kiran yar mutane da mayya kai tsaye, Haba inna.... kin san wannan ba magana bace karama kuwa??" Tagumi Inna tayi a hankali tace "Naga abinda ya isheni ni patuu... Me yasa Bukar ke min haka a rayuwa" Daddy yyi yace "Ni gaskiya nake gaya maki, kiyi hakuri ki daina wannan abinda kike ba shi da amfani, duk wanda kika ji bai maki ba sai kice masa maye?? Haba don Allah, ke kin xata maita karamin abu ne, wllh ki daina haka bai kamace ki ba kwata kwata, haka kawai ki dage kina ce ma yar mutane mayya ki dauko mana wata maganar, this is very wrong wllh" Shi dai Abba kansa na kasa, Inna dai bata kuma cewa komai tayi tagumi, kawu Audu yyi kasa da murya yace "Hajiya yanxu da xa a kai maganan nan gaba...." Tsawa tayi masa tace "Kai d'an tsut ka fita harkata, idan an kai sa gaba uwaka xa ayi?? kada wanda ya sani a bakin duniya gaskiya, da kansa ya kori matarsa ni ban koreta ba...." Shiru kawu Audu yyi bai kuma cewa komai ba, Mujaheed ne ya sakko parlon cikin kananun kaya, Abba ya daga kai yana kallonsa ko kiftawa babu ganin yanda ya rame, Daddy ma kallonsa ya dinga yi da mamaki, ya karasa parlon yyi kasa da kai ya gaishesu, Daddy yace "What's wrong with Muhd?" Ya d'an yi murmushi yyi kasa da murya yace "It's just malaria amma da sauki sosai Abba" Daddy yace "Are u under medication?" ya gyada kai yace "Sure sir" Kallonsa kawai Abba ke yi shi dai ya kasa cewa komai, Daddy yace "But did you have any problem Mujaheed, wannan anya Malaria ne kadai..." Inna ta tabe baki ta mike murya can kasa tace "Har da kamun mayya ko kun ki ko kun so" daga haka ta nufi kofa fuska daure, Daddy ya bi ta da kallon gefen ido, sai bayan da ta fita parlon gaba daya Abba yace "Me ya hada ka da matar ka kace ta tafi gida??" ya shafa kai a hankali yace "Abba...." Sai kuma yyi shiru, Daddy yace "Bama son jin komai my friend, get her back immediately, am I clear??" Mujaheed ya kallesa ya kasa cewa komai da farko, can a hankali yace "In sha Allah Abba" Kawu Audu yace "Toh xa mu je asibitin ne yanxu??" Mujaheed ya kallesa yace "A'a ina amsan medication a gida kawu, ai da sauki sosai yanxu" Kawu Audu yace "Toh Allah ya kara lafiya Muhd, Allah ya yaye maka" Mujaheed yace "Ameen" Mikewa Abba yyi yace "Ka dai ji abinda aka ce maka yanxu, get her back today, sannan I want you to try all possible means of stoping ur grandma from coming to this house" murmushin karfin hali Mujaheed yayi yana kallon Abban nasa, daddy yace "That's just it" Daddy na kallon Imaan dake xaune yace "Ke kuma mai nuna mata hanyar xuwa gidan ko?" Mujaheed ya kallesa da sauri yace "A'a Abba ta san hanya ai...." Imaan ta sunkuyar da kai bata ce komai ba, Daddy yace "Toh tashi mu wuce" Mikewa tayi ta nufi kofa, Daddy yace "Allah ya kara lafiya M.A" Mujaheed yyi murmushi yace "Ameen" Abba yace "Anjima ka taho gida tare da matar taka" yace "Toh in sha Allah" Kawu Audu yace "Sai ayi ta hakuri ka ji?" Murmushi kawai yyi ya sauke kansa kasa, har bakin mota ya rakasu, Imaan ta shiga bayan motar tana kallonsa tace "Allah ya kara lafiya" ya gyada mata kai kawai bai ce komai ba, Daddy ya shiga front seat, Abba ya shiga maxaunin driver yana kallon Mujaheed yace "An kawo kudin auren kanwarka, we will talk later idan ka xo gida" A hankali Mujaheed na gyada kai yace "Toh Allah ya sanya alkhairi...." Abba yace "Ameen" Mujaheed ya kara masu sallama suka bar compound din ya juya kamar me counting steps dinsa ya koma parlor ya xauna saman kujera ya jinginar da kansa jikin kujerar ya lumshe ido yana jin xuciyarsa na masa xafi. Umma na barin gidan tare da Safeenah dama bata yarda Safeenah ta tafi gidansu ba, ta lallabata da kyar suka wuce gidan Hajiya Saude, Hajiya Saude ta sauke ajiyar xuciya bayan Umma ta koro mata duk yanda aka yi, ita dai Safeenah sai hawaye take tana jin da yau xa a mika mata wuka daga ita sai Imaan a daki babu fa abinda xai hanata ta kasheta, bata taba jin tsanar mutum kamar yanda take tsanar Imaan ba, wai a kanta Mujaheed ya daga hannu ya mareta har sau biyu, for what??? Hajiya Saude tace "Kuma har sun kawo lefen koh???" Umma na share xufar da ke keto mata cikin tashin hankali tace "Wlh muna hanya Ummi ta kirani wai ga kaya an kawo, akwatuna har sha biyu da sadaki kusan miliyan daya, ni abun duk ya kwabe min wllh" Hajiya Saude ta bude baki tana kallon Umma, can tace "Amma wannan uwar yaron anyi tsinanniya, wato hauka ta manna mana wai xa tayi shawara" Umma tayi tagumi bata ce komai ba, Hajiya Saude tace "To yanxu meye abun yi kuma??" Umma tace "Auren nan fa ko ana ha maza ha mata baxa ayi sa ba in dai ni Rukayya ina da rai, wato sun ma ci bulus kenan da uwarta idan na hakura aka yi auren" Hajiya Saude tace "Gaskiya kam gashi daga ita ba wata balle ace a hakura xuwa wani lkcn" Umma ta mata wani kallo tace "Toh ko da wasu 'ya yan an gaya maki haka nan kawai xan bar imaan ta tafi gidan da xata huta, duk fitsara da rashin kunyar da kakarta ta dinga sa wa ta dinga min ya tashi a banxa ya tafi a banxa kenan, inaaa ai sai dai idan ban haifu cikin uwata Hadiza ba, Imaan sae dai ta ji labarin jin ddin aure amma ba dai ita ta ji ba" Safeenah ta tabe baki tace "Ni dai babban damuwata ta daina xuwa min gidana gaskiya, a kanta har Mujaheed ya daga hannu ya mareni kuma ki hanani gaya ma Hajiyata" Umma tace "Haba Safeenah bai kai ki gaya ma Hajiyar Marafa ba, kin santa da xuciya ki bar ni da shi kawai, kema kinsan haka nan baxai mare ki ba, wllh sai yayi da ya sanin abinda ya aikata, muna nan da ke" Safeenah ta yi tsaki bata ce mata komai ba, Umma tace "Tunda shawarar da kika bada aka yi amfani da shi kwanaki bai yiwu ba yanxu baki da wata shawarar da xa ki kara ba mu?" Safeenah tace "Don an kai lefe da kudin aure ba yana nufin anyi aure bane...." Shiru tayi ta bude jaka jin wayarta na ring, ta fiddo wayar tana kallon screen din, Kallon Umma tayi tace "Shi yake kirana" Umma ta xaro ido tace "Haba?? To dauka ki ji uban me xai ce maki" Safeenah ta wani daure fuska ta daga kiran ta sa handsfree tayi shiru, sallama yyi cikin sanyayyen muryarsa, cike da masifa tace "What did u want from me Mujaheed?" Ya d'an yi shiru sannan yace "I want to say I am sorry, kiyi hakuri tsautsayi ne" ta fashe da kuka tace "Tsautsayi ka daga hannu ka mareni a dakina a kan wata can, kuma a gabanta??" Yace "Nace kiyi hakuri, and take note Imaan ba wata bace kanwata ce, I see no reason xaki daga hannu ki mareta in kyale ki..." Safeenah ta bude baki ta xaro ido tana kallonsu Umma, tace "Wato kirana kayi ka sake min rashin mutunci kenan Mujaheed?" Murya can kasa yace "Not at all Safeenah, Kinsan Imaan ba lafiya sosai gareta ba, kuma ga grandma dinmu a gidan, da ban yi haka ba anything can happen... ni nasan halinta ke baki sani ba, so don't ever, I mean ever.... try giving her a bad look talkless of you laying ur hand on her face, xan iya maki fiye da abinda kika yi...." Sai kuma ya kwantar da murya yace "Yanxu dai I didn't call to talk long plss kiyi hakuri da abinda ya faru idan ma kince xa ki rama shkkn sai ki rama a kai na, but If you try touching my lil sis I will not take it likely with u" Bude baki Safeenah tayi da mugun mamaki tana kallon Umma da ta gwalo ido tana sauraransa ita ma, a hankali Safeenah tace "You called to warn me Mujaheed?" Yace "Not at all, na kira ne in baki hakuri, and tell me where you are now??" Umma tayi kasa da murya sosai tace "Kice kina gida wajena" Safeenah ta tabe baki fuska daure ta ki cewa komai, yace "Am asking kina Ina" alama umma ta dinga mata ta gaya masa tana can gida, ta harareta ta dauke kai tana wani cika tace "Ina gidan ku" Mujaheed yace "Good I am happy baki tafi gida ba, later da yamma xan shigo in sha Allah, I need rest now..." Daga haka ya katse wayarsa. Safeenah ta ja wani tsaki tana kallon Umma a fusace tace "Ni dai Hajiya kin bari kawai na tafi gidanmu Hajiyarmu ta san abinda ake ciki, aure ko wata uku ba ayi ba an fara mari na sbda wata shegiya, dubi fa hakuri ya kira ya bani amma dubi irin maganganun da ya dinga min da warning?? Infact wai ma me yasa baya ji da kanninsa haka yanda yake ji da ita?" Umma ta tabe baki tace "Uwar ce ta asirce min shi, tun yarinyar na yar karama tana yar yaye yake bauta da ita ke kya ce don shi aka haifota, nayi nayi in rabasa da ita amma inaaa, da yake kinsan lkcn a wajen kakar tasu yake, ita kuma yarinyar kullum sai an kai ta can sai ya maida ta gida da yamma, idan ba karyar kakarsu ba ma cewa tayi da sunansa ta fara magana, amma duk karya ce wllh, a haka dai ta taso ta makalkale ma d'a na sai kice shine Abubakar ubanta, idan kuwa xai dawo hutu gida daga Uk uban tsaraban da yake yo mata hankali baya dauka, kanninsa ko quarter dinsa basa samu wllh, wai ma don abun ya ragu sosai yanxu, ae ba karamin tashi tsaye nayi ba gaskiya, ban yi da wasa ba kam, kwanaki da dadewa fa mijin da Seeyama ke aure yanxu ya so hada imaan din da, kinsan abokinsa ne kuma yaron ga kudi ga hankali amma sbda shi shashasha ne wai da Imaan xai hada sa, ni ko na ruguje xancen gaba daya, shine yaron ya dawo ma Seeyama, yanxu wnn auren ma da ake son a mata shine gaba a kan komai ina jin, kuma bbu mamaki ya ma san yaron Bulasawan..." Safeenah da ke ta kallon Umma tace "Toh ni dai gaskiya tayi aurenta ta tafi gidan mijinta ta kyale min miji haka" Umma ta bude baki tace "Tayi aure kuma? To ai tunanin xata auri yaron Bulasawa ne yasa take raina mutane take ganin ita wata ce, wllh shi yasa take maki kallon hadarin kaji, kallon kowa take kasa da ita sbda tana tunanin yaron Bulasawa ne xai aureta, amma bata san she is mistaking ba, wllh wllh ba mijinta bane yaron in dai ina numfashi, ke kinsan ko gaisheni yarinyar nan da kike gani bata yi kuwa?? Uwarta kuwa jin ta take ita wata ce yanxu a dole ga ta surkar Bulasawa, to xa su kwashi kunyar su kuwa a hannu wllh ba cika baki ba" Safeenah ta tabe baki tace "To ae don an kai sadaki da lefe an sa rana ba shine yake nufin an daura auren ba, in dai ni take ma wani gani gani wllh ta tari aradu ba gamo... Sai na kunyatata in ga ta tsiya in ga karshen auren nata da shi Sadeeq Bulasawa din" Umma tace "Atohh, ni dai dama nace idan aka yi auren nan to fa ban haifu cikin uwata ba, daga ita har uwarta da kakarta sai sun kwashi kunyarsu a hannu ina kallo" Hajiya Saude tace "Kuna ta surutu ni ko har na gama yanke shawarar what next... Kuma in Allah ya yrda naji kamshin nasara...." Umma ta kalleta da sauri tace "Toh ba mu mu sha" Hajiya Saude tace "Amma duk da haka sai mun koma wajen mutumin nan ko xuwa gobe" Bayan Magrib Mujaheed yayi parking kofar gidansu ya fito ya kulle motar gaisawa suka yi da mai gadi dake bakin gate, Mai gadin na kallonsa yace "Likita ba lafiya ne" Mujaheed na kallonsa yyi murmushi yace "Alhmdllh, na ji sauki" daga haka ya shiga compound din, direct part din Inna ya nufa walking slowly, a hankali ya murda kofar parlon ya shiga, ido hudu suka yi da Imaan dake xaune parlon tare da Inna da ke ta fiddo kayan cikin akwatunan lefen da aka kawo bakinta har kunne, Ta Rasulu ma sai aikin fiddo ubansun kayan take tana cewa "Toh ga dai kaya ba laifi an xuba karyar naira, ko da yake suna da shi ne, Ni fa nasan har uwar Bulasawan nan a da wllh, don akwai wata makociyata kawar kanwarta da suke uwa daya tana ma uwar Bulasawan aikatau, lkcn ma kudin bai bunkasa haka ba, toh sai makociyar tawa ta ja ni wataran muka je gidan kawar kanwarta wai xata kai mu gidan kakar shi mijin Imaan wato uwar Bulasawa, sunan uwar tasa Hajiya Salamatu, tana nan wata doguwa fara, duka duka bata fa wuce mu ba amma kirkinta ragagge ne...." Inna dai sai kallonta take kasa kasa, ta Rasulu ta tabe baki tace "yo ragagge mana, a lkcn Ina goyon Shamsu daga ya mata fitsari a cafet, ga abinci mai lafiya da xuka xukan kaji an xubo mana xa mu ci in gaya maku abincin da ban ci ba knn don matar nan cewa tayi in tafi gida in canxa masa kaya xarni ya isheta, nan ko bata san har da kashi yyi ba ina ta boyewa ne har sai mun ci abincin, ni dai har da d'an kwalla na na bar gidan ina dukan shamsu, kafin in dawo kuwa su shafa'u suka side kwanon tass da ke kinsan dangin mayu ne, ni dai abincin ko a halshe na" Maimoon dai sai taya su fiddo kayan take bata ko kalli ta Rasulu ba, Duk suka kalli Mujaheed da ya shigo parlon ya tsaya yana bin akwatunan da kallo, Inna ta washe baki tana kallonsa tace "Mujaheed takwarata tayi goshi wllh, ko atamfar dubu ashirin Ina jin babu a nan, gwalagwalai kuwa mun kirga biyar da ta Rasulu, to me xance ma Allah banda in gode masa?" Imaan dai sai danna wayarta take, Mujaheed yace "Toh Allah ya sanya alkhairi" Inna tace "Ameen, kuma kayi hakuri da abinda iyayenka suka maka, ka dai fi su nesa ba kusa ba, in sha Allahu idan Allah yasa aka daura auren nan lafiya kai xaka kai Imaan har dakinta kayi mata fada sosai sannan mu taho gida mu bar ta" Dariya Maimoon ta dinga yi tana kallon Imaan da taki dago kanta, Inna ta tsuke fuska tace "Ke ba batun dariya bane, magana ta gaskiya shi xai kai ta gidanta... Ke kinsan wahalar da yyi da ita ne kuwa" Ta Rasulu tace "Wahala kuma ai ya tashi a banxa tunda ba shi xai aureta ba, kyansa ace wannan uban shakuwar da suka yi kawai ya aureta suje can su xauna tare, abinda ma ya fi kowa saninta a duniyar, ba shikenan sai su haifo santala santalan 'ya yansu su xube ma Aisha tayi ta bari barin da bata yi ba da, ku dai xumuncin ku duk kame kame ne ba shi da wani karfi Allah na tuba, Banda haka ba sai ayi tuwona maina ba ko don Rukayya ta hadiye xuciya ta mace, ita kenan fa gare Bukar a duniyar...." Tagumi Inna tayi kamar xata yi kuka tace "Ni dai naga abinda ya isheni ni Asabe... Wa ya gayyato min wannan mata??? Huuu gaskiya ta Rasulu kin lalace, ke kinsan uban sa6on da kika buga yanxu ki ja mana girgixan kasa kuwa? Kai wasu dai kyansu dawanau wllh" Ta Rasulu tace "Sa6o don nace da Mujaheed ya auri yar uwarsa Imaan? Ke dai baki son gaskiya, kuma baki tsoron Allah, Asabe kinyi watsi da tsoron Allahn ki tun tale tale, kai tun kina gidan Alhaji isuhu, kawai jin ki nake idan kince wasu basu tsoron Allah" Inna da ta wani tsuke fuska tace "To bari kiji, wllh da Mujaheed ya aure min jika gwara tayi ta xama ba aure ina kallonta, me xata ci da sauran Safara'u Allah na tuba?? Me xata yi da surka irin Rukayya ta6a66iya, ke ma dai wllh muguwa ce ta Rasulu, waye kuma Mujaheed da xa ki ce ya aurar min Imaan in shiga uku in lalace, Ina Imaan xata kai sa, ke dai wllh fitinanniya ce tirrrr" Mikewa Imaan tayi ta wani hade rai ta nufi kofa, Inna ta hade rai tace "Atoh maxa yi tafiyar ki Imaan kada a sa min ke a bakin duniya, Toh ni dai tunda kin gama ganin kaya tashi kiyi tafiyar ki ta Rasulu ba ruwana kar ki kawo mana rudani a lamarin mu, tunda ke rudaddiya ce, tashi ki tafi haka a gaida su Muhammadu" Ta Rasulu tace "Toh banda Mujaheed din dama wa xai iya da ciwace ciwacen Imaan Allah na tuba, ni fa tunda Uwar Bulasawa ta kore ni da d'ana ta hanamu abinci na tsaneta har yau" Inna tace "Toh ae ba ni da Ahmadu ta kora ba ta Rasulu, kuma ko da ni ta kora ma xuciyata me kyau ce fesss na yafe mata duniya da lahira, ke dai kawai kiyi ta kanki ta Rasulu, bikin ma ni bance lallai sae kin xo ba kar ki kunya ta ni don Allah ki rufa min asiri kiyi xaman ki a gida kin ji???" juyawa Mujaheed yyi ya fita parlon, Inna ta bi sa da harara tace "Waye kuma Mujaheed da xan hada jikata da?? Kai Allah dai ya isa da wannan tunanin naki gaskiya" Washegarin ranan Imaan suka fara jarabawan waec, karfe biyu saura suka tafi yin first paper dinsu, xuwa hudu da wani abu suka gama suka fito, tunda suka fito Maimoon ke kallon Imaan da ta nemi dakali ta xauna, Maimoon ta karasa kusa da ita tace "What happened Imaan?" Imaan ta kalleta a hankali tace "Kamar bana jin dadi" Maimoon tace "Toh sannu yanxu driver xai xo sai mu wuce gida" Mariya ta nufo su tace "Amaryar mu how was today's paper?" Imaan tace "Alhmdllh" Mariya tace "ki taso ku gaisa da Ya sadeeq yana waje, yace in kira ki" Imaan ta d'an turo baki tace "A'a ni dai kice masa baki gan ni ba plss" Mariya tace "C'mon ki taso mu je plss how will I say ban gan ki ba" Maimoon ta dago Imaan tace "Mu je kila ma Driver ya xo" Maimoon na rike da hannunta suka fita wajen gate din makarantar, a hankali Imaan ke tafiya har suka isa gun motar Sadeeq ta tsaya, ya dinga kallonta daga glasses din idonsa yace "What's wrong?" Mariya tace "Nima na tambayeta daxu tace ba komai" bude motar yyi ya fito yana kallonta daga sama har kasa yace "Me ke damun ki?" Kamar xata yi kuka tace "Ina yini?" Yace "I said what's wrong?" Ta sunkuyar da kai tace "I am not feeling fine" Back seat ya bude mata yace "Shiga in ajiye ki gida" ta buda ido sosai tace "Driver dinmu na xuwa" kallonta kawai ya tsaya yi, hakan yasa ta kalli Mariya, Mariya tace "Ki tafi xa mu taho yanxu" Sadeeq yace "Kema shiga mu je may be baxata yi tunanin guduwa xan yi da ita ba" dariya Mariya tayi tace "Toh kuma driver yana hanya, ku tafi kawai xa mu jira shi da su Ummi" ta fadi haka tana nuna masa Ummi dake can tsaye sai kallonsu take suna kallon direction dinta kuma ta dauke kai da sauri, a hankali Imaan ta shiga bayan motar, Mariya kuma ta shiga front seat, ya rufe motar ya xaga ya shiga maxaunin Driver ya tada motar suka bar kofar makarantar, tun da suka dau hanya yake kallonta ta madubi, ita ko ta jinginar da kanta ta rufe ido, har suka isa gida, parking yyi bakin gate yana kallonta ta madubi still, can ya bude motar ya fito ya dawo baya ya xauna, sai a sannan yasan bacci take da gaske, ya kai hannu forehead dinta ta bude ido da sauri ta koma baya, yyi kasa da murya yace "Ina ke maki ciwo?" Ta sunkuyar da kai tace "Ina jin xaxxabi" yace "Tun yaushe??" Tace "Da safe" shiru yyi bai ce komai ba, can ya sauka motar yana kallonta yace "Come down" a hankali ta fara sakkowa motar ya kama hannunta don taimaka mata, xata kwace hannun ya ki saketa, Bata yarda ta kallesa ba ta fito motar, yana kallonta yace "Anjima xan xo maki da drugs" tace "Toh nagode" saketa yyi ta juya xata shiga gate suka yi ido hudu da Mujaheed dake kallonsu yana xaune gun mai kiosk dake layin, ta dauke kai da sauri ta shiga gate din, duk da hada idon da Sadeeq yayi da Mujaheed shigewa motarsa yyi ya tada ya bar layin. Thanks for d call and text fans... Allah maimaita mana.... Ameen. *Imaan isn't for free* it's 300 via Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah Then u show ur evidence of payment via my WhatsApp number 07087865788Da daddare Imaan na parlon Inna a kwance ta dalilin kiranta da Sadeeq yyi xai kawo mata magunguna ita kuma bata son fita kofar gida shi sa ma ta taho part din Inna ya sameta a nan, ko tsinke Inna bata bari a parlonta ba cikin kayan da aka kawo na Imaan gaba daya ta kai su daki, dakin ma makulli take sa masa sai in xata shiga ta bude idan ta fito kuma ta kulle ta daure makullin a ha6ar xaninta, Inna dake xaune ta gama cin abinci kenan ta daura kafa daya kan daya ta ta6e baki tace "Ni dai da ki tashi ki lallaba ki koma can bangaren ku ki jirasa, bana son wannan juye juyen da kike min kamar macijiya gaskiya, ni bana son abinda xai gigitani da daddaren nan, Bukar kuma ba kirki ne da shi ba tsaf xai iya cewa a parlona ciwon ya tashi in shiga uku" Ita dai Imaan bata kulata ba, dai dai nan aka yi sallama kofar parlon, Mikewa Inna tayi tana amsawa tace "A'a Bisimillah Bukar, sannu da xuwa" Sadeeq ya shigo parlon, inna ta kinkimo lallausan carpet dinta da ta nade saboda masu shigowa kallon lefe kar su 6ata mata ta shimfida masa, yana murmushi ya xauna ya gaisheta, ta amsa tace "Tun daxu take xaxxabi nace ta tafi gidansu iyayenta su sani ta ki, to dama wannan mutumin Mujaheed da yana nan ne yasan kan xaxxabin, to ban gansa ba kuma nasa Maimuna ta kira min shi nace ga kanwarsa ba lafiya amma shiru bai xo ba, ita kuma lkcn da ba shi da lafiya har cewa tayi a fasa kawo lefenta da kudin aure sai ya ji sauki, su Ahmadu dai ne basu yarda ba, kowa da imaninsa kawai a rabu da shi, shi ya sani...." Sadeeq dake fiddo drugs da ya kawo bai dai ce komai ba, can ya kalli Imaan da ta juya masu baya, Inna tace "Atoh, tsorona daya kada uban yace a nan xaxxabin ya tasar mata kuma ni daxun nan ta shigo min wllh" a hankali yace "How are you feeling?" Shiru Imaan tayi bata ce komai ba, Inna tace "Idonta biyu wllh" Imaan ta hade rai ta juyo sannan ta mike xaune, ledan maganin ya nuna mata yace "Ur drugs with prescription, sai ki sha yanxu" Inna ta tafi kitchen ta dauko ruwan gora da cup tace "Toh tashi ki sha" Sadeeq yace "Ni xan koma Kaka" Inna tace "A'a abinci fa? uwarta ce tayi, da ke ni dama idan ba girkinta ba bana cin na kowa sai in Amina, tuwo ne da miyar agushi yaji kayan hadi, sai kamshi yake xubawa in xubo maka?" Yana d'an murmushi yace "Naci abinci kafin in taho kaka" tace "Toh ko in juye maka ka tafi da shi?" yace "Ai kuma ni da abinci sai gobe idan Allah ya kai mu" Inna tace "Atoh, haka naga Mujaheed ma yake yi, shi in dai karfe tara yyi bai ci abinci da daddare ba to ya gwammace ya kwana haka bai ci komai ba, kaji fa abinci ma sai an masa ka'ida, Ni ko nace aikin banxa, yo ko tsakar dare cikina ya bukaci hakkinsa bana tashi in san yanda nayi na sallamesa ba? Wlh akwai hisabi mai tsanani tsakanin mutum da yan hanjinsa, in dai ka cuce su to ranan gobe kiyama abun baxai maka kyau ba, shi sa ba ruwana ko biyun dare ne naji yyi kugi xan tashi in san abun yi, abinda ga kayan shayi kaca kaca a gidan" Sadeeq ya mike yana murmushi yace "Sai da safe kaka, xa a kiyaye" tace "Toh Allah ya bada ikon kiyayewa" Yana kallon Imaan yace "Sleep tight, Allah ya kara sauki" a hankali tace "Ameen, amma ba wanda xai sani bacci coz I am having 10 o clock paper tomorrow" yace "Not at all, xa ma ki iya tashi cikin dare kiyi karatun ki" daga haka ya nufi kofa Inna tace "Toh baxa ki tashi ki daddage kiyi masa rakiya ba Imaan?" yace "A'a ta sha magani ta kwanta kaka, sae da safe" Inna tace "Atoh, Allah ya tashe mu lafiya, ka gaida iyayen naka, Allah yayi albarka" yace "Ameen kaka nagode" daga haka ya fita parlon ya rufe kofar. imaan sun fara jarabawa da sati guda aka fara shirye shiryen biki a gidan kasancewar biki biyu ne da nata sai Ya Yusuf... yau Friday Imaan na dawowa exams karfe sha daya ta tafi part din Inna, bakin tap ta sameta tana wanke gaba daya buckets dinta da iron sponge da detergent, Imaan ta shiga parlor ta xauna, Sai kusan sha biyu Inna ta shigo tana cewa "Haka kawai, naga bokitai suna son komawa kamar takashin kare, Allah ubangiji ya min tsari, na wanke su tass na shanya kayana ni dai, kuma duk Maimuna ce me min amfani da abokitai gashi sun dauko hanyar dafewa, gaskiya xan kira ubanta ya mana iyaka, idan nata xai siya mata to sai ya siya mata ta rabu da nawa..." Tana kakkabe kujerunta tace "Toh ya jarabawan yau?" Imaan tace "Alhmdllh" Inna tace "Toh Allah ya baku sa'a, sai kiyi kokarin ganin kin cinye jarabawan kin fi kowa, to kin ci abinci kuwa?" Imaan tace "Ni bana jin yunwa" Inna ta tabe baki jin yanda take amsa mata ta gama kakkabe kakkabenta ta dauko tsintsiya, Imaan na kallonta tace "Inna Yaya yana xuwa?" Inna na gyara tsintsiyar hannunta tace "Yaya? Waye kuma Yaya?" Imaan bata ce komai ba, Inna ta tabe baki ta fara sharanta tace "Wai Yaya, to ajiyar Yaya kika bani Imaan? Ina xan ga wani Yaya mutumi na gidansa, ni har na mance rabon da ya tako min nan ma, toh mutumi ya fara sanin dadin aure me xai xo ya min kuma? A'a ni kam kusan sati kenan ban gansa ba" Imaan dai sai kallonta take, Inna ta kalleta tace "Sako xaki bada a ajiye masa?" Imaan ta turo baki tace "A'a kawai na daina ganinsa ne" Inna ta tabe baki tace "Toh ba sai ki shirya ki tafi gidansa ba ko akwai wanda xai hanaki? Ni dai har abada in taka cikin gidansa tunda iyayensa ba so suke ba, to me Mujaheed xai bani wanda Allah bai ban ba? A'a ba ruwana ta kai na nake yanxu, ni ko naje gidan nasa fa ko yar kudin motar nan baya bani, kullum a gantale nake dawowa idan naje wllh, to sai kace uwata tace min je ki kya gani" Imaan tace "Toh ki kirasa" Inna ta kalleta da sauri tace "In kirasa? Ke uban me ya hanaki kiransa, gafara xai min Mujaheed din koko?" Imaan ta hade rai bata ce komai ba, Inna ta ci gaba da sharanta tace "Ni dai kar ki dameni don Allah, waye kuma Mujaheed Allah na tuba" can kuma ta mike ta dauko wayar ta mika mata tace "Toh kirasa dai mu ji" Karban wayar Imaan tayi, tayi dialing number sa ta sa handsfree ta ba Inna, har ya gama ring bai dauka ba Inna ta ajiye wayarta ta ci gaba da abinda take. Ranan lahadi warce Anty ta kira domin yi ma Imaan gyaran jiki ta iso gidan duk da bikin saura sati uku, sati ukun kuma xata yi tana gyara Imaan, kudi ba na wasa ba Aunty xata biyata, matar ta so ace Imaan ko fita baxata dinga yi ba during the period amma hakan baxai yiwu ba sbda exams da take, Tunda Umma taga sananniyar mai gyaran jikin da aka dauko hankalinta yayi mugun tashi, duk gaba daya she is soo confused, sun koma gun mutumi kamar yanda Hajiya Saude tace amma ita fa taga abu sai gaba yake ga biki saura sati uku har xa a fara gyara amarya, tsabar yanda ta sa abun a rai har wani rama tayi abincin kirki bata iya ci, hatta bacci gagaranta yake yi ynxu, ga uban kayan abinci da drinks da aka fara jibgewa a gida na bikin... Anty ce xaune parlor tare da mata mai gyaran jiki tana sake jadadda mata irin gyaran da take so tayi ma Imaan, Matar tace "Baki da matsala Hajiya, ni tsakani da Allah nake aiki na" Anty tace "Toh sai abu na biyu, a wajen kakanta xa a ke gyaran, amma fa kinsan yanda tsoffi suke sai ana yi ana hakuri da kauda kai don Allah..." Dariya matar tayi tace "Ae muna da su Hajiya wannan ba damuwa bane in sha Allahu" Umma dake kitchen ta shirya xata fita amma ta kasa fita duk tana saurarensu, Anty tace "Toh mu je in raka ki bangaren kakar tata..." Mikewa matar tayi rike da Babban jaka, Anty ta dau mata dayan suka fita xuwa part din Inna, sai a sannan Umma ta fito tana danna wayarta, ta kai kunne, Mujaheed dake bedroom dinsa ya fito wanka yana shiryawa ya kalli wayar Safeenah dake gaban mirror yana ring, karasawa yyi ya dau wayar yana kallon screen din, har kiran ya katse kallon wayar yake ganin number Ummarsa, can ya ajiye wayar sai gashi ta sake kira, dauka yyi ya nufi kofa suka kusa cin karo da Safeenah xata shigo dakin, karbe wayar tayi a hannunsa tace "Ka gaji da kwanciyar kayi wanka kenan..." Bai tanka ta ba ya juya yana ci gaba da buttoning din shirt din jikinsa, ita kuma ta fita dakin ta koma nata don daxu da ta shigo ganin ko ya tashi ne ta bar wayar a dakinsa, ta daga kiran ta kai kunne tace "An tashi qlau Hajiya?" Umma tace "Lafiya lau, ya jikin Mujaheed?" Safeenah ta tabe baki tace "Ya warke fa kawai yana pretending ne sbda bai son ina xuwa inda yake tunda ina takurasa sai ya ci abinci ko makamancin haka, wllh har yanxu na rasa gane kan Mujaheed, gaba daya ya ki gaya min damuwarsa duk da dai da sauki yanxu, in dai ya fita aiki ne baya dawowa sai nayi bacci..." Umma tace "Ke ki rabu da shi haka nan yake ba a taba gano inda ya dosa, wani lkcn kuma tsabar miskilanci ne, ni da na haifi kayana kuma, kema ki fita harkansa kawai idan kika ga yana shan kamshi sai ki ga kun dawo dai dai..." Safeenah ta tabe baki tace "Ni ko ina xan sha masa kamshi ya hango wata a waje, gwara inyi ta lallabasa a haka...." Umma tace "Toh ni ba wannan ba, Safeenah shirye shirye dai sai gaba yake a gidanmu don yau ma aka dauko mai gyaran jiki xata fara mata gyara..." Safeenah tace "Saura sati uku fa Hajiya, ba sai a xuba ido ba a ga ikon Allah, idan fa mutum ya fiye axar6a6i da kyar ya dinga ganin abubuwa yanda yake so, ke dai kawai ki xuba masu ido ki daina damun kan ki, auren nan ance ko an daura bai fi na minti goma ba in ma an daura kenan to me xai dameki, ni ban cika yarda da irin mutanen nan ba amma gaskiya mutumin nan da alama yana da gaskiya sosai, duka duka nawa ya amsa wajen mu..." Umma ta sauke ajiyar xuciya tace "Ban son in sakankance ne da maganar mutumi a xo ayi abun nan Ina ji Ina gani, wllh da na shiga uku, shi sa gwara in buga nan in buga can, yanxu ma xan je gidan Hajiya Balaraba" Safeenah ta tabe baki tace "Toh ni dai sai mun yi waya xan hada ma mijina breakfast ya tashi" Bata jira cewar Umma ba ta katse wayar ta ajiye ta ja tsaki tace "Ance maki ba don abinda Mujaheed yyi min sbda yarinyar da irin rainin da take min xan bata lkcina a kan abinda ya dame ki ne, nima ta kaina nake shi sa na xage" shiru tayi tana imagining ace da gaske d'an Bulasawa ya auri Imaan, Tabb har takasu ma xata iya dinga yi ita surkar Bulasawa, kawai wataran sai a wani xo da motoci kusan biyar gidanta a sunan Imaan ce ta xo gaida Yayanta, ta sakko daga motar da gwalagwalai iri iri tana yatsine yatsine tana mata kallon banxa, tabbb, da sauri Safeenah ta kauda tunanin a ranta tana cewa Allah ya kiyaye hakan ma baxae faru ba, in sha Allahu talaka bawan Allah xa ki aura ki xo gidana in taka ki yanda nake so in walakantaki, murmushi Safeenah tayi wai ta hango imaan ta xo ce ma Mujaheed basu da abinci a gida shi kuma yace ta debo mata a nasu ta bata, Safeenah ta tabe baki tace "Ae Kyawunta ma baxai bari wannan mafarkin nawa ya xamo gaskiya ba, Allah dai yasa idan an rabata da yaron Bulasawan ba wani mai kudin xai kuma xuwa mata ba don wannan shine anyi ba ayi ba...." Safeenah ta d'an yi murmushi a ranta tace muna wargaza auren nan xa mu yi mata maganin bakin jini in sha Allahu, ita da aure sai dai taga wasu na yi, shiru tayi tana tunanin to kada kuma fa ta rasa miji wataran iyayen suce a hadata da yayanta tunda da aure tsakaninsu.... sosai gaban Safeenah ya fadi ta xauna gefen gado da sauri xuciyarta na bugawa, lkci daya ta girgixa kai tace "A'a gwara dai a rabata da d'an Bulasawan kawai, duk tsiyarta kuma baxata sake samun kamarsa ba sai dai kasa da shi" murmushi Safeenah tayi ta mike ta fita dakin dai dai fitowar Mujaheed daga bedroom dinsa, rungume sa tayi tana shigewa jikinsa tace "What should make for breakfast sweetheart?" Tabe baki yyi ya kauda kai. Sosai Imaan tayi wani fresh tayi kyau ta dalilin gyaran da aka fara mata, har wani sheki da glowing skin dinta yake, duk ta gifta ka dama kamshin da xaka ji na musamman ne, a haka kuma take fita tayi jarabawa kullum, tun biki na saura sati biyu dama wayarsu ya ragu sosai da Sadeeq, yawanci kuma ita ke kiransa ma, shi ko sai dai ya bi miss call dinta. Yau Wednesday Imaan na dawowa daga exam bayan tayi wanka ta sauya kaya Inna ta xubo mata abinci da yaji nama ta ajiye mata a kusa da ita tace "Ni dai wai yaushe xa ku gama wannan kaddararren jarabawan ne ki nutsu waje daya a maki gyaran nan cikin kwanciyar hankali, wannan ae fitina ne ana gyara yana bin iska tunda kullum sai kin fita..." Imaan na kallon abincin da Inna ta ajiye mata tace "Ni fa bana jin yunwa" Inna ta kalleta da sauri tace "Ni dai na shiga uku da wannan 'ya ta Bukar, ko kumallon kirki fa baki yi ba daxu, a haka xa a kai ki gidan Sadeeq din nan da sati biyu a rame duk k'ashi a wuya?? Ni dai ba ruwana bari Amina ta shigo tunda Aisha ta sallama mata ke gaba daya" Imaan ta tura abincin xata kwanta kan kujera a fusace Inna tace "Ni fa bana son a dameni gaskiya sai ince ki tattara kayanki ke da mata mai gyara ku koma bangaren ku yanxu nan, ya xan dinga maki magana kina walakanta ni, dama katuwar mata mai gyaran jiki ce tace ki ci abinci kafin ta dawo taje siyo wasu kayayyaki a kasuwa ta dawo, to idan ta dawo ba ki ci ba fa..." Imaan tace "Inna to ko dai yaya ba shi da lafiya ne har ynxu?" Bude baki Inna tayi tana kallonta da mamaki, can ta xauna tayi tagumi a hankali tace "Naga abinda ya isheni ni Asabe, waye kuma Yaya??" Imaan ta turo baki ta dauke kai, Inna tace "Wai akwai abinda ya hada ki da Mujaheed ne bayan kasancewar Ubansa wan ubanki? Akwai wani dangantaka tsakaninku ne dama da ban sani ba? Wato kwana biyu shiru bai shigo ya takura ki ba shine duk kika damu tunda ke gantalalliya ce, toh sai ki tashi ki tafi gidansa, Toh wai ma ina ruwanki da wani yaya ke da xa ki yi aure nan da kwana sha biyar? Ko dai akwai ajiyar ki a gunsa ne bai baki ba kafin a kai ki daki in kirasa ya baki?" Imaan ta wani hade rai tace "Toh kawai daga tambaya? Naga ya dade bai xo ba kuma ba haka yake ba" Inna tace "Toh idan lalacewa yyi ya fara hakan fa?? Ko idan ya xo me xai bani banda ya tsokane ki ya cuce ki ya wuce don ma naga tunda yayi aure yyi hankali ya daina sa ki kuka, Ke dai ki dinga jin tsoron Allah kiyi ta kanki ba ruwana, to ni ko shekaranjiya na sa Ummi ta kira min shi katon ya ki dauka, wa ya sani ko fushi yake na daina xuwa gidansa, sai kace gidan aljanna Allah na tuba, ni dai ba ruwana wllh" daga haka Inna ta shige daki, imaan ta bi ta da harara ta jinginar da kanta da kujera bata ce komai ba.... Ana saura kwana 7 biki Imaan ta gama jarabawa kasancewarta science student, Maimoon da Mariya kuma nan da kwana shidda xa su gama jarabawan don art class suke, yau kusan kwana hudu basu yi waya da Sadeeq ba, bai kirata ba ita ma bata kirasa ba, tana bedroom din inna bayan la'asar hannunta rike da hisnul Muslim wayarta ya fara ring, daukar wayar tayi tana kallon mai kiranta, ganin number Sadeeq ta daga ta kai kunne tayi shiru, shirun shi ma yyi na kusan second goma sannan yace "How are you?" Murya can ciki tace "Am good" yace "Ina waje" ta kalli agogo bata dai ce komai ba, yace "Or are you busy?" Tace "Ni ba bari na ake ina fita ba..." Ya d'an yi shiru sannan yace "What did you mean?" Tace "Bana fita" yace "Ohk gida ake biyo ki da papers din ki kenan?" Turo baki tayi tace "Waye ubana da xa a biyo ni gida da papers?" Yace "What exactly are you trying to say?" Kin cewa komai tayi, Yace "Ohk then kar ki fito..." Xai katse wayar frnd dinsa Saleem dake tsaye gefensa jikin motarsa ya amshi wayar ya kai kunne yace "Haba amarcy ba dadewa fa xa kiyi ba, ki d'an fito pls, just few minutes" a hankali Imaan tace "Toh" Saleem ya katse wayar yana kallon Sadeeq yace "Amare fa lallaba su ake basa laifi Dr" Sadeeq dai bai ce komai ba yana rungume da hannunsa, Saleem yyi murmushi yace "To saki ran kafin ta fito mana" Nan ma dai Sadeeq bai tanka sa ba, Hijab Imaan ta saka sai dai ba har kasa ba, ta fito parlor ta sanar ma Inna sadeeq na kiranta a waje, Inna dake xaune parlon tare da mai mata gyaran jiki suna hira sai kallon takwarar tata take, can a hankali cikin sanyin murya tace "Ashe dama haka kike da kyau ban sani ba Imaan?" Dariya sosai mai gyaran jiki ta shiga yi tana kallon Inna dake sa ta nishadi tun xuwanta, kwata kwata bata gajiya da fadan Inna da labaranta masu kai da marasu kai, ga uwa uba tsaftarta, komai na Inna burgeta yake, Imaan bata san lkcn da tayi murmushi ba bata dai tanka Inna ba ta nufi kofa ta fita, Inna na kallon mai gyaran jikin tace "Allah kuwa yar nan, dubi fa yanda take walkiya da kyalli, ga kamshi kaca kaca ta ko ina a jikinta, duk inda ta gilma sai ya kamu da kamshin da take yi, ni dai xan kara maki dari biyu da tsinkin sabulu a kudin da xa su biyaki, gaskiya kin fito min da jikata, kai har dambun nama xan maki ni dai" Matar dai sai dariya take tana ma Inna godiya, Imaan na isa part dinsu ta shiga don daukan hijab mai tsayi, Ammi ta fito daga kitchen jin an bude kofa, Imaan ta gaisheta sannan ta nufi dakinta, Ammi ta bi tada ido, ba a dau lkci ba ta fito sanye da hijab har kasa, tana kallon Ammi a hankali tace "Ana kirana a waje ne..." Shiru Ammi tayi tana kallonta, hakan yasa Imaan ta sunkuyar da kanta, Ammi ta karaso kusa da ita ta sa ta xauna saman kujera ta xauna kusa da ita tace "What's wrong with you Imaan?" Imaan ta kalleta da sauri tace "Ba komai fa Ammi" Ammi tace "Noo there is something kar ki ji komai ki gaya min..." Imaan ta girgixa mata kai a hankali tace "Da gaske ba komai Ammi...." Ammi tace "Toh shikenan, but don't forget baki da wanda ya wuce ni a duniya, idan baki gaya min damuwar ki ba ban san wanda xa ki gaya ma ba" Imaan ta sunkuyar da kai tana murmushi tace "Idan akwai xan gaya maki ai Ammi" Ammi tace "Toh ki kwantar da hankalin ki and keep praying, kar ki gaji da addu'a, kuma ki dinga cin abinci sosai kin ji" murya can kasa Imaan tace "Toh nagode Ammi" Ammi tace "Ko me kike bukata ki kirani a waya ki sanar min" Imaan tace "Toh bari in je ana jirana" Ammi tace "Toh ki kame kanki" mikewa Imaan tayi ta nufi kofa Ammi ta bi ta da kallo har ta fita ta kulle kofa. Tunda Imaan ta iso part din su Maimoon Umma dake xaune tare da Hajiya Balaraba kan fararen kujeru take kallonta ko kiftawa babu, ta sunkuyar da kai ta gaishesu a hankali Hajiya Balaraba ce kadai ta amsa a dakile, tuni kamshin da take ya daki hancinsu gaba daya, har ta fita gate basu daina kallonta ba, Da ba don Saleem da ya ki barin sa ba da tuni Sadeeq ya bar wajen ganin har bayan minti goma bata fito ba, tana fitowa sau daya ya kalleta ya ci gaba da danna wayarsa, Saleem ya mata murmushi har ta iso inda suke ta tsaya a gefe a hankali tayi masu sallama sannan ta gaishesu kanta a kasa, Saleem ya amsa yace "Hope an gama exams lfya?" Tace "Alhmdllh" Sadeeq ya maida wayarsa aljihu yana kallonta ta cikin glasses din idonsa a takaice yace "Wani shirin xa ku yi a nan gida?" Shiru tayi da farko, sai kuma ta kallesa taga wani direction yake kallo daban, tace "Nima ban sani ba" yace "Ohk then, on Thursday xa ayi dinner...." Yana magana ya bude mota ya fiddo hadadden IV mai yawa sosai ya mika mata ta risina ta amsa, shi dai bai yarda sun hada ido ba, yace "I think that's all, dama sbda IV din na xo, if there is anything I will call and let u know" daga haka ya bude driver seat ya shiga, ita dai sai kallonsa take, Saleem na mata murmushi yace "Toh mun gode amarya, ki shiga ciki xa mu koma" tayi murmushin karfin hali ta juya ta nufi gate, Saleem ya xaga ya shiga front seat, Sadeeq ya tada motar suka bar layin, suna hawa kan titi Saleem yace "Plss ka rage wnn xuciyar Sadeeq... I don't like the way u treated her gaskiya" Sadeeq dai sai driving dinsa yake bai ce masa komai ba, Saleem ya tabe baki ya fiddo wayarsa yana dannawa, Sadeeq yace "Raina min hankali take" Saleem yace "Meye abun rainin hankali" a d'an fusace Sadeeq yace "Baka ji abinda tace ba kenan, wai bata san abinda xa su yi ba a gida na biki, wato babu events da xa su yi kenan take nufi, which is a lie" Saleem ya tabe baki yace "Duk wannan xumudin da ka dinga yi kwanki kafin a saka bikin duk naga babu shi yanxu Sadeeq" Sadeeq ya rage gudun da yake yana shafa kansa a hankali bai dai ce komai ba.... *Imaan isn't for free* it's 300 via Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah Then u show ur evidence of payment via my WhatsApp number 07087865788cRanan lahadi da karfe sha daya Mama Hadiza ta iso gidan tare da autar ta Maryam, a part din su imaan suka sauka as usual, sai bayan azahar sannan suka taho part din Inna, Inna dake xaune ta gama hada ma Imaan kwadon rama da ya ji kayan hadi a bowl kenan tayi masu kallo daya ta dauke kai ta rufe bowl din raman ta ajiye a gefe, Maryam ta tabe baki ta xauna tana kallon TV, Mama Hadiza ta xauna kusa da Inna tana murmushi tace "Sannu Innata" ba tare da Inna ta kalleta ba tace "Yauwa, a rufe min kofata kada k'uda su biyo bayan ku su shigo min parlor" Mama Hadiza ta mike ta rufe kofar ta dawo ta xauna tana murmushi tace "Ina yini Inna? Fatan mun same ku lafiya" Inna tace "Lafiya lau, ai naji labarin tun sassafe ku ka shigo nan dai ne ba ku xo ba sai yanxu" Mama Hadiza tayi dariya tace "Mun d'an kintsa ne Inna, ya shirye shirye?" Inna tace "Atoh suna can suna yi, ko shawara ma basa yi da ni wllh ban ya ake ciki da maganan bikin ba, nasan dai ta Rasulu xata gayyato kawayenmu gaba daya sai a kafa mana katon rumfan nan da kujeru mu xaxxauna a tsakar gida" Mama Hadiza ta sunkuyar da kai tana murmushi, Inna na kallon Maryam tace "Toh ita wancan har yau ba manema ne yarinya ta xama sangamemiya ban ji ana batun aure ba Hadiza, kina gaba tana biye da ke fa a baya" Maryam ta hade rai ta gaisheta, Inna tace "Lafiya lau, baki da samarin ne?" Maryam dai bata ce komai ba ta dauke kai, Mama Hadiza dai sai murmushi take tana kallon uwartata, Inna ta tabe baki tana gyara daurin dankwalinta a hankali tace "Ni dai ba ruwana" Mama Hadiza tace "Toh Ina amaryar, ango dai shi ya dauko mu airport daxu?" Inna tace "Isuhu ai ya lalace ya daina shigo min nan kwata kwata sai dai mu ci karo a tsakar gida, Ita kuma Imaan suna can bandaki tare da mata mai gyaran jiki, ke kya ce canja mata fata xata yi, ni kada garin neman ido a rasa gira a kona min jika in shiga uku, iyayin matar yyi yawa wllh, gashi duk tayi ta ajiye min kaya ta ko Ina kamar tababbiya, ni ko in tattara in jibge mata su a kan katuwar jakarta, ni dai na gaji wllh" Dariya Mama Hadiza ta dinga yi, can tace "Mujaheed fa inna?" Inna ta kalleta tace "Ai Mujaheed ya daina xuwa gidan nan, ni na fi wata ma ban gansa ba, ba laifin xaune balle na tsaye ban san me na masa ba ya dauke kafa" Mama Hadiza ta fiddo wayarta a jaka tace "Toh yanxu ai dole ya xo, jiya ma mun yi waya da shi kafin in taho..." Tana magana tayi dialing number Mujaheed, har ya gama ring bai dauka ba, Inna tace "Atoh, ko dai an sace wayar tasa ne, nima har na gaji da kira ba a dauka fa" Imaan ce ta fito daki sanye da Hijab har kasa, ta wara ido ganin Maryam ta nufeta da sauri ta rungume ta cike da jin dadin ganinta, Maryam ta wara ido tace "Waoww sis kinga yanda kike glowing kuwa? Wllh kin yi kyau sosai" Imaan na murmushi ta koma gun Mama Hadiza ta durkusa ta gaisheta, Mama Hadiza ta jawota jikinta smiling broadly tace "Maa sha Allah, my daughter kinyi kyau sosai, ya shirye shirye" Imaan ta boye fuskarta jikinta a hankali tace "Lafiya lau mama" Inna tace "Ai dama ita Imaan da kyanta, wannan gyaran kyanshi dama Ummi, ita ce mummunan gidan, gaskiya ban san inda Rukayya ta samo ta ba..." Dariya Mama Hadiza tayi tana kallon Inna, Inna tace "Allah kuwa" Mama Hadiza na kallon Imaan tace "Toh tafi ki goge jiki ki shirya" Imaan ta mike tana murmushi ta wuce daki Maryam ta bi ta da kallo don kyau ba na wasa tayi ba. Imaan na xaune tare da Maryam a bedroom din Inna bayan la'asar, Maryam dake ta kallonta a hankali tace "Kina nufin ba events da xa ayi Imaan?" Imaan ta bude hannu tace "Nima ban sani ba sai dai ki tambayi Maimoon, daxu dai ya kawo IV, su xa suyi dinner" Maryam tace "Toh dress code fa? Kuma wani kayan yace xa ki sa?" Imaan tace "Oho ni bai gaya min ba" Maryam tace "Kamar ya, ba ku shirye shiryen tare ne?" Imaan ta tabe baki kamar baxata ce komai ba, sai kuma tace "Ni ko waya fa bama yi" da mamaki Maryam tace "Saboda me?" Imaan tayi shiru tana kallonta, Maryam ta kamo hannunta tace "Talk to me, what's happening?" Imaan ta sauke idonta tace "Nima ban sani ba, baya kirana sai dai in ni na kirasa, kuma ba xuwa yake ba" Maryam ta xaro ido tana kallonta da mamaki, Imaan ta d'an yi murmushi tace "In xubo mana abincin ynxu?" Maryam tace "Plss mu yi magana ki ajiye batun abinci, toh ke kina ga babu abinda kika masa Imaan?" Imaan ta girgixa kai a hankali tace "Ba abinda na masa wllh, he just changed all of a sudden, I don't know why...." Sai kuma tayi shiru lkci daya hawaye ya kawo idonta, Maryam ta kasa daina kallonta lkci daya jikinta yyi sanyi, can cikin sanyin murya tace "Kuma kin tambayesa abinda kika masa? Kila kin yi offending dinsa baki sani ba" Imaan tace "That doesn't warrant him to change his attitude, ko don yaga few days ya rage a daura mana aure shi sa yake min haka" sai kuma ta fara kuka a hankali, Maryam taji gaba daya hankalinta ya tashi ta rungumeta tace "Plss kar kiyi kuka, we have to find out why d sudden change of attitude, be strong plss" Imaan dai bata ce mata komai ba, bayan wani lkci ta mike a hankali tace "Bari in xubo mana abinci" daga haka ta fita dakin. Bude Ido Sadeeq yyi don ganin wanda ya shigo masa bedroom dinsa that is almost out of bound for everybody except his mum, Mikewa xaune yyi yana kallonta, Mummy tace "Sai yaushe xaka kai masu kayan da ka bari parlor na ga lokaci na ta wucewa Abba, today is Tuesday, or do they have any other alternative?" Yace "Mum xan ba Mariya ta kai anjima" Da mamaki Mummy tace "Mariya kuma, kaga ina involving din su a harkata a gidan nan?" Sadeeq ya koma ya kwanta yace "Kawarta ce fa Mum, ta san gidansu ai, I don't think I am going out today" Mummy tace "You tell me what's wrong with you this days Sadeeq, meye matsalar ka" Mikewa xaune yyi yace "Mummy frankly speaking gaba daya naji bana son auren nan kuma, am I even supposed to get married now? Isn't it too early? Sure Ina sonta amma bana son auren ynxu gaskiya" Wani kallo ta dinga masa, kafin tace "You are stupid..." tashi yyi ya wuce bathroom ya rufe kofar gbam, ta fi minti biyar tsaye dakin mamaki fal xuciyarta kafin ta juya ta fita. Sadeeq ne xaune parlon Dad dinsa da yammacin ranan, tun shigowar sa parlon bai yarda ya daga kansa ba, Mummy ma na xaune parlon sai kallonsa take, Alhaji Ahmad Bulasawa dake tsaye ya gama duk fadan da xai yi kamar xai ari baki daga karshe ya xauna yana kallon Sadeeq da kyau yace "If you think I have a son that will tarnish my image here in my mother's land... you are mistaken Abubakar, ban haifi wannan d'an ba, kindly get out from my sight now, aure ba fashi tunda ba wani ya nema maka yarinyar ba, kuma ba wani yace ka fito da xancen aure ba yanxu" A hankali Sadeeq ya mike ya nufi kofa ya fita parlon Mummy ta bi sa da kallo, Alhaji Ahmad yace "In sha Allah daurin aure babu fashi ranan juma'ah..... No one is tarnishing my image" direct Sadeeq part din Step mum dinsa ya wuce, Aunty na dakinta ya sameta, ta ajiye abinda take yi tana kallonsa tace "Ango kayi scarce, ya shirye shirye" ya karasa kusa da ita ya xauna ya rike kansa, da mamaki tace "Me ya faru Abba?" Da kyar ya dago yana kallonta da idanuwansa da suka kada yace "Pls Aunty kiyi ma Abba magana a daga bikin nan, wllh naji gaba daya am not ready to be a family man, wani lkcn sai ayi amma ba yanxu ba" Bude baki Aunty tayi tana kallonsa, da wani expression tace "Are you alright Sadeeq? Kana da hankali kuwa, biki saura few days kace a daga, waye kake son maidawa kananun mutane, ubanka dai koh? Kai ma kasan Abban ka will never support this, wani laifi fatiman tayi maka ne?" Ya girgixa kai a hankali yace "Ni bata min komai ba, kawai naji bana ra'ayin aure yanxu, ba cewa nayi a fasa ba, a daga kawai nake so... " Aunty ta saki baki tana kallonsa with much surprise, can ta girgixa kai tace "Don Allah ka rufa mana asiri, kada ka maida mu kananun mutane a idon jama'ah Abba, haba Sadeeq this is very unusual of you, me ya same ka haka, ko dai gantalallun frnds dinka ke xuga ka??" Rasa ma me xai ce mata yyi, can ya mike kawai ya fice daga dakin ta bi sa da kallo baki bude. Mummy ta gama hada duk kayan da suka ma Imaan kala uku masu tsada, daya na dinner biyu kuma na events idan xa su yi a gida, immediate din Sadeeq Annur ta samu a dakinsa ta mika masa tace "Gashi ka kai ma yayanka yana garden, kace nace ya tafi ya kai masu yanxun nan" daga haka ta fita dakin. Bayan Magrib Sadeeq yyi parking kofar gidansu Imaan ya kashe motar ya fito ya dau ledan kayanta dake bayan motar, ya fi minti biyar tsaye jikin motarsa ya ki kiranta a waya, can kawai ya shiga cikin gidan kamar mai counting steps dinsa, direct part din Inna ya nufa, yayi sallama bakin kofar parlon, Inna ce ta amsa sannan ya shiga, Mama Hadiza dake xaune parlon tana cin abinci suna hira da Hajiya Bilki mai gyaran jiki, ta rufe abincin ta ajiye gefe ganinsa, Inna ta mike ta shimfida masa darduma tana masa sannu da xuwa, sauke kansa yyi kasa yana d'an murmushi ya ajiye ledan hannunsa ya xauna a hankali ya gaida su gaba daya, Mama Hadiza ta amsa tace "Sannu da xuwa Sadeeq..." yace "Kun xo lafiya mama?" Tace "Alhmdllh, ya shirye shirye?" Yace "Alhmdllh" Inna tace "Kaga yanxu kuwa ta fita taje raka wannan yarinya Maryam su gaisa da Ahmadu ko a kira maka ita a waya?" Yace "A'a kaya ne dama na kawo mata" Inna tace "Atoh ai shkkn sai in ajiye mata, kana dai cin abinci kuwa Bukar naga kai ma ka fige kamar amaryar taka" murmushi yyi ya sunkuyar da kansa yace "Ina ci Kaka" da damuwa Inna tace "Aa ku dai yi hakuri ku kwantar da hankalin ku ko kwa yi kyan gani da biki don Allah..." Shi dai bai ce komai ba, Bude kofar parlon aka yi Mujaheed ya shigo da sallama, sanye yake cikin kananun kaya hannunsa rike da makullin mota, Tunda ya shigo Mama Hadiza ke kallonsa, yyi murmushi yana shafa kansa ya karasa cikin parlon, sai da ya fara ba ma Sadeeq hannu sannan ya xauna kusa da Mama Hadiza a hankali yace "Kun xo lafiya mama?" Ta rike ha6a tace "Kayi rashin lafiya ne ba a gaya min ba Muhd?" Yace "Ae naji sauki yanxu, kwanaki ne nayi rashin lafiya, tare da Maryam ku ka xo?" Inna dake kallonsa da kyau tace "Toh dai yau ga ni, ga Mujaheed, ga Hadiza da katuwa mai gyaran jiki, ga kuma yaron nan Sadeeq, sai Mujaheed ya ji tsoron Allah ya fito ya gaya ma kowa abinda na masa a parlon nan yanxun nan... Don ni ban san abinda na masa ba, idan Mujaheed bai saka min da abun kirki bautar da na masa ba yana yaro ai baxai guje ni ba yanxu da tsufa na, Hadiza yau kusan wata shidda kenan ban sa Mujaheed a ido ba, ba laifin tsaye balle na tsaye, ba lafin fari balle na baki, ko na kirasa baya dauka to ni dai gaskiya ya fito ya fadi abinda na masa ko in bar sa da Allah..." Ko kallonta Mujaheed bai yi ba sai juya makullin hannunsa yake, Hajiya Bilki dai sai dariya take kasa kasa, Mama Hadiza ta kasa cewa komai sai kallon Inna take ganin yanda ta ci serious ta tsuke fuska, Sadeeq dai idonsa na kan wayarsa da yake dannawa, cikin rawar murya Inna tace "Ko don nace matarsa mayya ce ya kullace ni ban sani ba, toh banda haka me na ma Mujaheed, wllh ban masa komai ba, ko wani kaga xai mance da ni haka a rayuwa kai ba mai tare min bane balle kai da kanka, gashi duk ka wani fige kamar kazar Hausa kuma ace yarinya ba mayya bace.... Ni dai ba ruwana" Mujaheed na kallon Mama Hadiza yace "Ba ku taho da su El-Ameen ba?" Mama Hadiza ta sauke ajiyar xuciya tace "Xa su taho tare da babansu xuwa jibi, xai xo daurin auren shi ma" Inna ta bude baki tace "Toh shi Mujaheed ba mutum bane da ya ki xuwa nasa daurin auren?" Mama Hadiza tayi murmushi tace "Inna kar ki manta Imaan ita kadaice gun Yaya, banda haka ma da ba lallai nima in xo ba tunda yaushe na xo bikin Mujaheed, to wannan dalilin yasa babansu Maryam ma xai xo daurin auren nata...." Inna ta tabe baki tace "Ku dai ku dinga tsoron Allah, ku dinga abu saboda Allah, wato shi Mujaheed bai cancanci a xo nasa ba sai na Imaan, to ubansa ya sha Mama ya bar ma ubanta, duk babu wani banbanci" dariya kawai Mama Hadiza tayi bata dai ce mata komai ba, shi dai Sadeeq idonsa na kan wayarsa, Maryam ce ta fara shigowa parlon Sadeeq ta fara gani ta gaishesa da fara'a, ya amsa yana murmushi yace "Kun xo lafiya Maryam?" Tace "Alhmdllh Dr, ya shirye shirye" yace "Lafiya lau" ta wara ido ganin Mujaheed tace "Ya M.A..." Imaan ta shigo parlon hannunta rike da fruit salad da Ammi ta bata ta kawo ma Mama Hadiza, ganin Mujaheed xaune parlon ta tsaya tana kallonsa ko kiftawa babu, daga kai yyi ya kalleta, bata san lkcn da ta ajiye bowl din hannunta ta nufesa da sauri ta xauna kusa da shi tana kallonsa ta wara ido tace "Yaya..." Ya shafa kansa kamar baxai ce komai ba sai kuma ya d'an ja hancinta yace "Kanwar Yaya..." dariya ya bata, ganin yanda take dariya yyi murmushi yana kallonta, rungumesa tayi a hankali tace "I missed you" Kallonsu kawai Sadeeq yake, Mama Hadiza ta dinga ma Imaan wani kallo amma imaan ko sanin tana yi bata yi ba, Inna tayi tagumi ta rasa abun cewa sai yan idanuwa, Can a fusace tace "Ke dai gantalalliya ce wllh, katuwa da ke ki fada jikin mutumi wai Yaya, yanxu fa ke matar wani ne, da ba don mijin naki ya san alakar ki da Mujaheed ba me kike tunanin xai faru yanxu? Kawai mata daga shigowa ki dare kan mutumi kice Yaya???" Da sauri Imaan ta sake Mujaheed ta juyo, sai a nan suka yi ido hudu da Sadeeq, sosai gabanta ya fadi ta xamo kasa tana kallonsa, Mama Hadiza dai ta kasa cewa komai amma gaba daya kunya ya isheta, Inna tace "Toh waye kuma Yaya Allah na tuba ke ba yarinya ba yanxu, mutumi yyi aurensa kema xa ki yi naki, ai kuma sai a hakura haka sai 'ya yanku su ci gaba da xumuncin, ni dai ban taba ganin haka ba...." Sadeeq ya d'an yi murmushi ya mike yace "Kaka ni xan koma yanxu" Inna tace "Au to baka sha ko ruwa ba Bukar" yace "Ae daga gida nake Kaka" Inna tace "Toh shikenan Allah maka albarka, kuma ka dinga cin abinci kaji" yace "In sha Allah" Yana kallon Mama Hadiza yyi kasa da kai yace "Mama xan koma, Allah huce gajiya" Mama Hadiza tace "Toh ka gaida mutan gidan Sadeeq na gode kwarai" kofa ya nufa, Inna na kallon Imaan tace "Ae sai ki tashi kusa da mutumin nan ki tafi ki sallami mijin ki koh" Kin tashi Imaan tayi, Mama Hadiza na ganin Sadeeq ya fita tace "Baxa ki tashi ki fita ba shashashar yarinya, kawai ki kama ki rungume mutum a gabansa sbda baki da natsuwa" a fusace Inna tace "A'a ke kuma bana son fadan rashin gaskiya, wa gareta da xata rungume banda Mujaheed din, a haka suka taso abun su dama can, shi ma mijin ai ya sani, ko ce maki aka yi bai sani ba, sarai ya san yayanta ne bata da kamarsa a duniya ko kun haifa mata wani yayan ne ban da shi Mujaheed din?? Ni bana son fadan rashin gaskiya wllh, kinsan yaushe rabon mu sa Mujaheed din a ido ne? kuma ta gansa baxata nuna farin cikinta ba, kullum sai ta min xancensa don ma Ina gwaleta kamar bai dameni ba alhalin kullum da daddare sai nayi mafarkinsa, kawai mata daga xuwa ki hau yar mutane" Hajiya Bilki ta dinga dariya tana kallon Inna, a hankali Imaan ta mike ta bi bayan Sadeeq Mujaheed ya bi ta da ido. *Imaan isn't for free* it's 300 via Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah Then u show ur evidence of payment via my WhatsApp number 07087865788A hankali Imaan ke tafiya tana kallon Sadeeq da har ya kusa gate sbda saurin da yake, kafin ta fita kofar gida har ya shiga motarsa ya wuce, ta bi motar da kallo sannan ta juya a sanyaye ta koma part din inna, Mama Hadiza dai har lkcn ta ki sake fuska don ba karamin 6ata mata rai abinda Imaan tayi yyi ba, tana shigowa parlon kuwa ta dinga hararanta fuska daure, Imaan na ganin haka ta sunkuyar da kai ta wuce bedroom din Inna duk jikinta yyi sanyi, Inna ta bi ta da kallo sai kuma ta kalli Mama Hadiza tace "Toh ba shikenan ba har ta sallamesa ta dawo, amma kina neman maida karamar magana babba sbda rashin tsoron Allah, ai shi Sadeeq din ya fi kowa sanin tsakaninsu da Mujaheed, kuma yaro ne mai hankali da natsuwa, tunda nake ban taba ganin yaro natsatstse irin sa ba, gashi kwata kwata abun sa bai rufe masa ido ba, kyauta yake kamar bai san ciwon dukiyar ba, to bayan ni har ku ma baxa ku huta ba aka ce maki Hadiza??" Ita dai Mama Hadiza bata ce komai ba tayi tagumi, Inna ta tabe baki tace "Ni dai ba ruwana... A dinga kyakkyawan xato domin Allah, sai kace warce ta fada kan wani kato can a titi, wannan ae yayanta ne Mujaheed" Mujaheed ya mike yana kallon Mama Hadiza yace "Toh na gaishe ki Mama Allah ya huce gajiya sai na shigo gobe" Inna na kallonsa tace "Amma kai dai Allah ya xuba maka shegen rowa Mujaheed kamar uwarka, banda haka ina laifin ka riko mata Yar gasasshen kazar nan da yar lemo... ka wani shigo gansansan daga kai sai kai, inda Isuhu ya fi ka kenan gaskiya" Mujaheed dai bai tanka ta ba ya nufi kofa, tace "Toh nayi magana daxu baka ce komai ba, ina fa da labarin abinda kayi ma Seeyama lkcn bikinta, to ita Imaan ko don ba ubanku daya ba, naga har yanxu shiru baka yunkuro ba, kyansa dama kawai ka bata kudin ni nasan abinda xan mata da shi, kar ka siya mata komai ba abinda Ahmadu da Bukar basu yi mata ba, kudin xai fi mata amfani gaskiya" ya juya ya kalleta yace "In xan bata abu ae ba sai kin sani ba Hajiya, sai kace mahaifiyarta bata kusa....." Daga haka ya fice daga parlon Inna ta rike ha6a tana kallon Mama Hadiza tace "Ke me yake nufi kenan? Kaddai baxai ma yar uwarsa komai ba bikinta sukutum da guda?? To bari dai in xuba ma saurautar Allah ido, amma wllh in har Mujaheed bai bada gudunmawa mai kauri bikin Imaan ba lalacewa ta samesa duniya da lahira, kuma ban san da wani idon xai kalli ubanta ba" Washegari laraba da safe driver ya ajiye su Imaan saloon, Mai wajen da kanta tayi mata gyaran bayan ta gano amarya to be ce, Banda kallonta babu abinda ake yi a saloon din, don gaba daya she looks so new, tayi wani haske da fresh sai glowing ko ina na jikinta yake kamar balarabiya, dubu ashirin Abba ya basu na gyaran gashin su uku don Ummi da Rahma basu yarda sun biyo su ba, da kyar Maryam ta lallaba Imaan ta yarda ayi mata kitso a gashinta, imaan har ta mance rabon da tayi kitso, haka aka ta daure aka rangada mata kitsonta kanana mai kyau, sai kusan azahar suka kira driver ya xo ya maida su gida. Sosai gida ya cika da jama'ah na kusa da nesa duk da sai Juma'ah ne bikin amma kai kana ganin jama'ahn gidan kasan only child ce xa ayi ma aure, kuma ga biki ya hade biyu, gaba daya yan uwan Ammi suna gidan, daga su har 'ya yansu, Aunty ma duk yan uwanta na kusa da nesa sun iso, Bakin ciki kamar xai kashe Umma, kwata kwata taki yarda ta fito daga dakinta har da sa makulli daga ciki abun duniya ya taru ya mata yawa, anya auren nan baxa ayi sa ba kuwa?? Tambayar da ta dinga yi ma kanta kenan, wata xuciyar na assuring dinta baxa ayi ba ta xuba ido kawai. Su Imaan na komawa gida da awa daya mai lallin da Aunty ta kira ta xo gida yi mata lalle, Inna ta gama xuba ma imaan pepper soup din da Aunty ta aiko mata da abinci kenan mai lallin ta shigo tare da Maimoon, Maimoon tace "Inna mai lalli ce" Inna ta kalli mai lallin da damuwa tace "Naga jaraba, ko abinci fa bata ci ba kika xo lalle baiwar Allah.... Tun safe take garari a titi wai gyaran gashi ynxu kuma daga ta fito wanka na xuba mata abinci sai ki xo kice kin xo lalle baiwar Allah, ba fa ta ci komai ba" Mama Hadiza dake parlon ta kalli mai lallin tace "D'an yi hakuri ta ci abinci yanxu ta gama Aunty..." Mai lallin tace "Toh xan jirata a waje" daga haka ta fita, Inna ta harari Mama Hadiza ta gefen ido ta dau abinci ta tafi daki kai ma Imaan tana cewa "Abu dai munafurci munafurci ba a son fadin gaskiya, na ma mata maganar gaskiya kin kwantar da murya kina mata magana salon ta min kallon fitinanna" Imaan ta gama saka kaya kenan Inna ta shigo tace "Ki ci abincin ki a nutse kafin ki fito wani shegen lalli, ba ruwana da gantalewa, ko lallaba maki lallen bana yi da kaina ba cikin dare" daga haka Inna ta juya ta fita. Maryam na kallon Imaan dake tsakuran abincin da Inna ta ajiye mata tace "Ki bani number Sadeeq in kirasa ai shi ya kamata ya baki kudin lalle da kitso ba su Abba ba" Imaan ta kalleta, sai kuma tayi murmushi tace "A'a just leave him... There is no need ai Abba riga ya bada" Maryam tace "Like seriously tun xuwan mu kasar nan ban ga ya kiraki ba Imaan, there is something wrong somewhere bai kamata kiyi shiru ba gashi jibi daurin aure ki cuci kanki" Imaan ta tabe baki tace "Am not saying anything Maryam, kika san uxurinsa" Maryam tayi shiru tana kallonta da mamaki, Imaan ta mike ta rufe abincin don gaba daya ta kasa ci, tun last week tayi loosing appetite dinta gaba daya, a hankali Maryam tace "Baki ci komai ba a abincin Imaan" Imaan tace "Mai lallen tana ta jirana, anjima xan ci" daga haka ta fita dakin, Maryam ta bi ta da kallo, bayan few minutes ta dau wayarta ta shiga duba number Sadeeq, tana gani tayi dialing, har ya gama ring bai dauka ba, ta sake kira nan ma bai daga ba, kwashe lambar tayi a nata wayar ta ajiye ta mike ta shiga gyara ma Inna daki, tana gamawa ta dawo ta xauna ta dau nata wayar tayi dialing number din Sadeeq, ba a dau lkci yana ring ba ya daga, shiru tayi da farko sai kuma tayi masa sallama, ya amsa, tace "Sadeeq?" Yace "Yes..." tace "Why the sudden change of attitude toward ur financee Sadeeq?" Ya d'an yi shiru kafin yace "Wait! Who is this?" Tace "You answer my question first..." Yace "I don't think you are in the rightful place to..." A d'an fusace tace "Kar ka gaya min magana malama, wato kai a silly thought dinka ka riga da ka sameta xaka fara walakantata tun bata shiga gidanka ba ko?? to wllh karya kake Imaan ta fi karfin haka, you are mistaken malam, domin ka kawo sadaki kuma jibi daurin aure ba yana nufin har ta xama taka ba...." Ya katse ta shi ma yace "Toh ki ce mata tayi xuciya ta gaya ma iyayenta ta fasa auren kawai, sai su maido min da sadakina.... I think this will be better than you calling and saying nonsense on phone to me madam" daga haka ya katse wayar, Maryam ta dinga kallon wayar da mugun mamaki nan ko xuciyarta cike yake da tantamar anya Sadeeq din da ta sani ne wannan, Anya Sadeeq din da ya siya mata latest phone da take mafarkin mallaka kwanaki da suka xo Nigeria kawai don tayi masa addu'ar Allah ya bar sa da Imaan ne wannan, mikewa tayi very shock ta fita dakin, a parlor ta tadda imaan mai lalli na mata lallin, Inna ta matsar da kujerunta gaba daya ta lullube su, ta kwashe carpet dinta kada a goga mata lalli a cuceta kamar yanda tace, Xaunawa Maryam tayi tana kallon Imaan, lkci daya taji tausayinta ba kadan ba ya kamata, kawai mikewa tayi ta fice daga parlon daga karshe.... Sai kusan Magrib Imaan ta wanke lallenta da yyi kyau ba kadan ba ta tafi part din su dauko Hijab don Inna ta wanke mata gaba daya wanda ta taho da, Shirye shiryen Mothers day da xa ayi gobe kawai ake yi a gidan, bata ga kowa part din su ba ta wuce daki ta dauko hijab ta fito, Muryar Maryam taji tace "Imaan" da sauri ta kalli direction da taji muryata ta ganta xaune ita kadai a dinning, karasawa tayi tana kallonta tace "Me yasa kika ce baxa ki yi lallen ba?" A takaice Maryam tace "Nothing" Imaan tace "Amma fa jiya kince xa ki yi" Maryam tace "Fasawa nayi, xauna mu yi magana Imaan" Imaan ta ja kujera ta xauna tana kallonta, Maryam ta d'an yi shiru sai kuma tayi kasa da murya tace "You know what imaan?" Imaan ta girgixa mata kai gabanta na faduwa, Maryam tace "Plss ina son ku xauna da Inna kiyi mata magana yanda xata fahimce ki, ki ce mata don Allah tayi ma su Abba magana a daga bikin nan xuwa wani lkci" Kallonta kawai imaan ke yi, Maryam ta girgixa kai tace "This is not the Sadeeq you know before imaan, ki rufa ma kanki asiri ki yi ma Inna bayani ita kadai xata iya ma su Abba magana su daga bikin nan, wllh idan kika auri wannan Sadeeq din you are going to live a miserable life in his home, gaba daya gadara yake yana ganin ya gama samun ki, dama boye maki real him yyi tun farko, kinsan yanda muka yi da shi a waya daxu da na kira in ji dalilin Change of attitude dinsa?" Imaan da har hawaye ya kawo idonta ta girgixa mata kai a hankali, Maryam tace "Ce min yyi ince maki idan kin isa ki fada ma su Abba kin fasa auren a dawo masa da sadakinsa" Sosai gaban Imaan ya fadi ta dinga kallon Maryam xuciyarta na bugawa, Maryam ta girgixa kai cikin sanyin murya tace "I am not in support of you marrying Sadeeq any longer Imaan, ba shi da mutunci ko kadan, hallaka ki kawai xai yi Imaan, kiyi hakuri ko min son da kike masa ki samu Inna ki gaya mata abinda ke faruwa a san abun yi tun da sauran lkci..." Imaan ta fara kuka a hankali, cikin sanyin murya tace "But I love him Maryam, shi ma yana sona, I just don't know what came over him..." Sai kuma ta fashe da kuka sosai ta hade kanta da dinning cikin rawar murya tace "May be stress yasa yake jin haushi haka, ni dai nayi masa uxuri, this is not the Sadeeq I use know, nasan idan munyi aure xa mu koma yanda muke da in sha Allah...." Da mugun mamaki Maryam ke kallonta tace "Are you on ur right senses Imaan, Ina gaya maki ga abinda mutumi yace kice idan kunyi aure xa ku dawo yanda ku ke da???" Imaan ta dago tana kallonta hawaye na sakkowa idonta tace "Ina sonsa a haka Maryam, kawai ki taya ni da addua Allah ya maida sa yanda yake da, beside bayan duk bak'in da suka taho from different places sai ace an fasa aure, idan shi bai fito ya fada masu ya fasa ba I see no reason why I should do so Maryam" Mikewa Maryam tayi tana mata wani irin kallo tace "Baki da hankali wllh" Imaan ta tashi da sauri tace "Plss this should be between us, ban ga dalili me karfi da xai sa ince na fasa auren nan ba, don Allah forget you even called him, ai ni xan xauna da shi ba ke ba, I know he loves me, nima kuma Ina sonsa, so plss mu bar maganan nan a nan" daga haka Imaan ta bar dinning din Maryam ta bi ta da kallo baki bude. Daren ranan Imaan bata yi bacci ba, gaba daya she is just disturbed nd restless, ta mike xaune daga karshe ta kalli Inna dake sllh kamar dai yanda ta saba duk dare, kallon agogo tayi taga biyu da minti biyar, wayarta ta dauka tana kallo, sai kuma ta shiga text message, cikin minti goma ta gama rubuta ma Sadeeq text, da farko tambayarsa tayi ko tayi masa wani laifi ne ya gaya mata, daga karshe kuma ta basa hakuri cikin tausasan lafazi ta tura masa, tagumi tayi tana kallon wayar duk da bata expecting reply don tasan bacci yake at that time, text taga ya shigo wayar nata gabanta ya fadi sosai, ta dinga kallon wayar kafin ta dauka ta bude text din tana kallon content dinsa, "if you think you notice any change of behavior da bai maki ba a tattare da ni, ki yanke hukunci da kika ga is the best, wanda xai yi suiting din ki" ta karanta text din ya fi a kirga amma ta kasa apprehending, can ta yi dialing numbersa har ya gama ring bai dauka ba, ta kuma kira bai dauka ba, ta tura masa text na cewar ya dau call dinta don Allah, ba a dau lkci ba reply ya shigo yace "Good night" Ta dinga kallon reply din sannan ta ajiye wayar ta mike ta shige bathroom ta rufe kofa, kuka ta fara yi a hankali tana jin xuciyarta na mata xafi, tayi kukan da ta dade bata yi ba amma maimakon taji d'an sanyi a ranta sai k'una da radadi, bubbuga kofa Inna tayi tace "Me kike yi a bandaki tun daxu Imaan, lafiyan ki??" Imaan ta fara wanke fuskarta da sauri, Inna bata fasa bubbuga kofar ba hakan yasa imaan ta bude kofar kanta a kasa, Inna ta gwalo ido tace "Kukan uban me kike? Ni fa bana son a gigitani gaskiya, ni ba karamin aiki na bane ince ki bi dare ki koma gidan ku, lafiya kike kuka a bandaki" Imaan bata tanka ta ba ta fara alwala, Inna tace "Naga jaraba, don xa a maki aure kuma sai ki shige bandaki kiyi ta kuka salon cuta ta kama ki" inna na tsaye tana kallonta har ta gama akwala ta fito ta sa hijab dinta ta hau saman darduma, Inna ta tabe baki tace "Ni dai ba ruwana" daga haka ta tafi ta xauna ta ci gaba da addu'o'in da take. Washegari tun sassafe Umma ta bar gida ana girke girke, ko danginta daya babu a cikin mutanen da suka cika gida, Ummi da Rahma ma duk ta sa sun shirya sun bar gidan, Aunty mamaki ta dinga yi na irin xuciyar umma, tunda take bata taba ganin mata mai nuna bakin ciki kiri kiri a fili irin Umma ba don cikin anko hudu da suka yi da Ammi ko daya ta ki yi, su Ummi ma ta ki barin su dinka nasu da aka masu. Mama Hadiza ce xaune parlon Inna tare da Aunty misalin tara na safiyar ranan Thursday din, Inna na kallonsu tace "Toh dama so nake ku rufa min asiri ku tattara 'yarku ku maidata can bangaren ku, tun daren jiya take kuka ga idanuwa can sun kumbure, toh ina dalili wani abun ya sameta a bangarena, dama aure hauka ne, wannan mata mai gyaran jiki ba irin lallashin da bata mata ba amma kamar ana tunxurata, to tunda uwarta ta sallama maku ita shi sa na kira ku, ku tafi da ita can nayi kokari haka kuma Allah ya gani" Aunty ta mike ta tafi dakin inna tana kallon Imaan dake kwance, murmushi tayi ta xauna kusa da ita ta dagota tace "Haba daughter, kuka kuma haka?? Ko kina da damuwa ne?" Imaan bata ce komai ba ta sunkuyar da kanta, Aunty tace "Kiyi hakuri kar ki sake kuka kinji, it's always like this for every lady Imaan" Imaan ta fara wani sabon hawayen, Aunty ta rungume ta tana lallashinta, Mama Hadiza ta shigo dakin ita ma ta dinga kwantar mata da hankali, sai da suka tabbatar tayi shiru gaba daya sannan suka fita dakin, Aunty ta hado mata shayi mai kauri ta kai mata. *Imaan isn't for free* it's 300 via Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah Then u show ur evidence of payment via my WhatsApp number 07087865788Bayan azahar mai make up da aka yi hiring ta xo tayi ma Imaan very light make up da ya fito da ainahin kyanta na 'yar fillo, ta saka wani lace mai tsadan gaske da Daddy yyi mata da head din da xata saka, ko tsinke ba a taba ba a lefenta dama, gaba daya kayan da xata yi fitan biki Daddy ne yyi mata su, tayi kyau har ta gaji barin ita da dama bata make up, kowa sai kallonta yake cike da sha'awa, Aunties din Sadeeq da Step mum dinsa duk sun xo gun mother's day din, Mariya da frnds dinsu na islamiyya da boko duk sun xo suma, da Ammi da Aunty ankon lace suka yi, ko kai ka gansu sai sun burge ka, karfe uku da wani abu Umma ta dawo gidan ita ma ta shirya cikin tsadadden lace ta shigo cikin jama'ah ana ta gaisawa, sosai hakan ya ba Aunty mamaki sai dai bata ce komai ba, bayan kusan awa daya sai ga Safeenah ta xo gidan cikin shiga ta alfarma da sisters dinta biyu, can kuma sai ga wasu daga kawayen Umma, gida ya cika da frnds din Aunty da Ammi masu ji da kansu cikin ankonsu na mothers day da Aunty ta fitar, irin rawan da Safeenah tayi sai abun ya baka mamaki, don xagewa tayi ba kadan ba kamar dai bikin masoyiyarta, sosai hakan ya ba Imaan mamaki, ita dai tana xaune ana ta abubuwa a wajen, duk Ammi na lura da imaan throughout the program bata da walwala kana gani kasan tana da damuwa, biyar da wani abu Ammi ta samu ta kebe da ita a backyard din apartment dinsu tana kallonta tace "Imaan ba nace ki kwantar da hankalin ki ba, or do you have any problem da baki son fada min ne" Imaan ta girgixa mata kai cikin sanyin murya tace "Ba komai Ammi...." Sai kuma ta sunkuyar da kanta hawaye ya fara taruwa idonta, Ammi tayi tunanin kila duk fargaban da ko wace amarya ke yi da xulumin barin gida ne ke damun yar tata, hakan yasa ta jawota kusa da ita ta shiga kwantar mata da hankali cikin taushin murya, Imaan dai sai gyada mata kai take hawaye na sakko mata, Ammi ta rungumeta tace "Bana son wannan kukan Imaan, today is ur happy day, ki saki ranki pls" a hankali imaan tace "Na daina" Ammi tace "Good ki shiga ciki ki xauna, karfe nawa yace xa ku tafi dinner din?" ta girgixa kai tace "Ban dai sani ba kila bayan Magrib" Ammi ta bude mata kofar kitchen tace "Go in and get some rest before then, or are you feeling pain anywhere?" Imaan ta girgixa kai tace "A'a" Ammi tace "Toh shiga ciki ki xauna" shiga kitchen din tayi sai kuma ta juyo a hankali tace "Ammi Daddy na fa?" Ammi tace "Ya dawo two days ago ai, don kina part din Inna ne" Imaan tace "Toh" daga haka ta wuce dakinta, wayarta da ta sa a jaka ta fiddo tana dubawa taga text na Sadeeq, sosai gabanta ya fadi ta bude message din tana kallon content dinsa, "I am sorry to let u know that... tonight dinner isn't going to hold anymore due to some reasons, ki sanar ma mutanen gida, thanks" ta karanta message din ya fi sau biyar sannan ta ajiye wayar a sanyaye, lkci daya ta ji wani hawaye me xafi na xubo mata, xaunawa tayi gefen gado ta cire head tie dake kanta, Maimoon ta kira a waya daga karshe ta sanar mata babu dinner din ta gaya ma su Ammi don a sanar ma mutane da xa su tsaya sbda dinnern, Maimoon tace "What?? Sbda me??" A hankali Imaan tace "Ke dai ki gaya masu kawai ni ina daki yanxu" daga haka ta katse kiran, Aunty ce ta shigo dakin tana kallonta tace "Imaan shi Sadeeq din yace maki babu dinner kuma?" Imaan ta kalleta trying her best to look alright tace "Ehh daxu yyi min text Aunty, he said he is sorry for the inconvenience" Aunty tayi shiru tana kallonta can tace "Toh shkkn Allah ya so babu wanda ya tafi can din ma" daga haka ta fita dakin, kowa a gidan yayi mamakin me yasa aka ce an yi canceling dina, ciki har da Umma dake tsakar gida tace "Ahhh gaskiya mu dai ba a kyauta mana ba, mu da muka sa ran mu yi yanda muka ga dama yau abu namu maganin akwabe mu, ni fa har na hango an dire ma kowa full chicken a table da lemon masu kudi, gaskiya an shiga alhakin mutane da yawa..." Safeenah tace "Ikon Allah, to bari mu san inda dare ya mana dama dinner din nake xaman jira a tafi, ni ban ma taba jin inda aka fasa dinner ba sai a bikin gidan nan" Ammi dai ko kallonsu bata yi ba tana sallaman wasu frnds dinta da gifts da aka raba na mothers day, Mama Hadiza tace "Toh ai gwara hakan, Allah na tuba meye abun birgewa a dinner, albarka ake so a aure dama ba tsiya ba, dinner sai kace fadan Allah, ai ni wllh ya burgeni da yace bbu dinner kowa sai ya ci kajin a gidansa...." Umma dai bata kalli inda take ba ta shiga sallaman neighbors dinsu da xa su tafi, Mama Hadiza ce ta tafi sanar ma Inna babu Dinner don suna can ana shiri da ta Rasulu da taxo da yamma, Inna ta gwalo ido tana kallon Mama Hadiza tace "Subhanallahi shi Bulasawan wiwi ya sha da xai ce an fasa shagalin?" Mama Hadiza dai bata ce mata komai ba ta fita, Inna ta kalli Ta Rasulu da har ta fiddo kayan da xata saka da mayafi tace "Yau naga gantalallen mutumi ta Rasulu, wai ki ji ba casu" Bayan isha Imaan na xaune can karshen gado tana ta bin frnds dinsu da Mariya dake ta hira a dakin da kallo, ko kadan bata san abinda suke cewa ba don gaba daya she is absentminded, Maryam dai na xaune one side tana danna wayarta amma gaba daya mood dinta wasn't good, Maimoon ce ta shigo dakin ta nufo Imaan ta mika mata wayar hannunta, Imaan ta amsa a hankali tace "Waye?" Maimoon tace "Ya M.A" Imaan ta kai wayar kunne tayi sallama, cikin sanyin murya Mujaheed ya amsa mata daga daya bangaren, tace "Ina yini Yaya?" yace "Lafiya, can you pls come out now?" Tace "Kana Ina?" Ya d'an yi shiru sai kuma yace "Ki sameni bayan apartment dinmu" tace "Toh" daga haka ya katse wayar, ta mika ma Maimoon wayarta ta sauka daga kan gadon ta dau hijab dinta har kasa ta saka, Maryam na kallonta tace "Where are you going to?" Imaan tace "Yaya ke kirana" daga haka ta fita bayan tace ma su Mariya tana xuwa, ta kitchen dinsu ta fita, ta dinga tafiya kamar mai tausayin kasa har ta kai Bangarensu Maimoon, tsaye ta gansa yana facing bango har ta iso kusa da shi bai juyo ba, a hankali tace "Ga ni Yaya" juyowa yyi yana kallonta, lkci daya ya sauke idonsa, ya fi minti biyu bai iya yace komai ba, sai kuma cikin sanyin murya yace "Sure I was suppose to ask you what u want for ur wedding but I didn't Imaan, but I don't know if you will appreciate this little that I have for you..." Imaan dai sai kallonsa take, wani round box mai kyau dake hannunsa ya bude yana kallonta ya fiddo bracelet sai kyalli yake kana gani kasan na menene ya kamo hannunta a hankali ya saka mata a wrist cikin sanyin murya yace "Am hoping you will love it lil sis" lkci daya hawaye ya kawo idonta ta fada jikinsa tana shessheka tace "Nagode Yayana" rungumeta yyi cikin breaking voice yace "I am... wishing u all d very best in ur marriage lil sis, Allah ya ba ku xaman lfya, but.. but i want to let you know this Imaan....." Sai kuma ya kasa ci gaba ya runtse ido, saketa yyi ya janyeta jikinsa ya juya xai bar wajen tace "You want to let me know what Yaya?" Bai juyo ba sbda bai son taga hawayen idonsa yace "I want to let you know that, kiyi ma mijin ki biyayya, be the best wife you can..." Daga haka ya wuce ta bi sa da kallo tana goge hawayen idonta tace "Toh nagode Yaya" a hankali ta juya ta koma apartment dinsu hawayen da take ta gogewa ya ki tsaya mata. Kamar Daren jiya wannan Daren ma Imaan bata yi baccin kirki ba, sai kallonsu Mariya da Maimoon da Maryam dake ta baccinsu take, daga karshe ta tashi ta dauro alwala ta dinga sllh har sai da taji bacci ya xo mata, nan kan darduman ta kwanta nn da nan kuma bacci yyi awon gaba da ita. Da asuba Ammi ta shigo ganinta kwance kasa ta tada ta tana kallonta tace "A kasa kuma Imaan maimakon ki tafi dakina?" Imaan ta mike xaune tana murxa ido tace "Sllh nayi ne daxu" Ammi tayi shiru tana kallonta, can tace "Toh ku tashi ku yi sllh lkci yyi" daga haka ta fita dakin, Da safe gida ya xamo ba masaka tsinke duk inda ka bi jama'ah ne, tun asuban fari dama ake ta girki a gidan don Aunty tace da kansu xa su yi abinci ba sai an wani kira masu yi ba, Umma ma dai na cikinsu, da ita aka dinga yin komai tun asuban, Ba karamin tilasta Imaan Ammi tayi ba ta sha shayin da ta hado mata sannan mai make up tayi mata make up kamar jira, yau ma dai wani ubansun lace din ta saka da ya fi na jiya, Maryam kam cewa tayi kanta na ciwo don ma kada a tilasta ta saka kaya, da ta tuna yanda suka yi da Sadeeq jiya sai ranta yyi mugun baci, in kuma ta tuna abinda Imaan ta gaya mata wai ba ruwanta sai tayi wani murmushi tana tausayin Yar uwar tata, Maimoon da Mariya suka cakare cikin ankonsu na ranan aka dinga hotuna. Karfe sha daya Yusuf ya fito dakinsa xuwa parlon Abba ta dalilin kiransa da yyi a waya, gaisawa yyi da mutanen dake parlon nasu don tun safe yake daki da few frnds dinsa, da sallama ya shiga parlon Abbansa yana kallonsa ya xauna yace "Gani Abba...." Abba xai yi magana Daddy ya shigo parlon da sallama, Yusuf ya gaishesa, Daddy ya amsa gaisuwarsa sannan ya xauna yana kallon Abba yace "Ina hanya ka kirani Barrister..." Abba ya kalli Yusuf yace "Kaje waje ku shigo tare da Sadeeq, ya kira yana waje...." Yusuf yace "Sadeeq Bulasawa?" Abba yace "Ehh" mikewa Yusuf yyi ya fita, Daddy ya kalli agogo sannan ya kalli Abba yace "Why is he here?" *Imaan isn't for free* it's 300 via Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah Then u show ur evidence of payment via my WhatsApp number 07087865788Tare Yusuf suka shigo parlon Abba da Sadeeq, Sadeeq yyi kasa da kai ya cire glasses din idonsa ya xauna saman rug ya gaishesu cikin sanyin murya, amsawa suka yi a tare suna kallonsa, Yusuf ya xauna shi ma yana duban Sadeeq da ya ki dago kai, calmly Abba yace "Hope all is well Abubakar?" Sadeeq bai ce komai ba kuma bai dago kansa ba, daga daddy har Abba kallonsa kawai suke, Yusuf ma haka, Can Sadeeq ya dago kansa ba tare da ya yarda sun hada ido da ko daya daga cikinsu ba a hankali yace "I am sorry I am saying this late, ina son don Allah ku min alfarma ayi hakuri da daurin auren nan yau saboda wasu dalilai...." Kallon mamaki Abba da Daddy suka shiga yi masa, Yusuf da ya xaro ido shi ma ya dinga kallonsa, Sadeeq ya shafa kansa murya can kasa yace "I think I am not ready for marriage now, I am sorry I am saying this at the die minute, but this is just d fact, ku yi hakuri...." Yusuf na masa wani kallo ya mike a mugun fusace yace "How dare you say such at this time, who do you think you can take for granted here...." Abba da gaba daya Sadeeq ya gama kulle masa kai cikin cool voice yace "What exactly are you trying to tell us here now Sadeeq.... What do you mean?" shiru Sadeeq yyi bai ce komai ba, can ya kallesu yace "I think it's good a fasa auren nan sai wani lkcn, ku min afuwa...." mikewa Daddy yyi cikin tsawa yace "You are very stupid...." Abba ya mike da sauri ya nufi d'an uwan nasa sanin xuciyarsa yana kallonsa a nutse yace "keep calm Abubakar, keep calm..." Mikewa Sadeeq yyi kansa a kasa yace "I am sorry..." Daga haka ya nufi kofa ya fita daga parlon, Yusuf ya bi sa da kallo da mugun mamaki, "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un" shi ne kalmar da Abba ya dinga furtawa ya kasa tsaye waje daya, daddy ya koma ya xauna a hankali trying his best to be calm, Abba ma ya koma ya xauna har lkcn yana nanata Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, silent din kusan minti biyar ne ya biyo baya a parlon, kowa da tunanin da yake a ransa, can Abba ya daga kai ya kalli daddy, lkci daya wani tausayin d'an uwan nasa ya rufe sa, how will such thing happen to his only child, cikin sanyi Abba yace "Look Abubakar you need not to worry, haka Allah ya tsara kuma Alhmdllh, I am sending them their pride price immediately, sannan plss do not say anything to anybody about this yet...." Daddy dai bai ce komai ba ya jinginar da kansa da kujera ya lumshe idonsa, Yusuf duk jikinsa yyi sanyi ya ma kasa kallon iyayen nasa ya rike kansa kawai, Abba ya mike walking round as if looking for a solution, sosai xaka ga damuwar dake tattare a fuskarsa, Daddy ya mike daga karshe calmly yace "Bani sadakinsu in mayar masu yanxu Barrister" sanin halin daddy yasa Abba yace "Xan maida da kaina Abubakar, ba sai ka je ba" duk ynda daddy yyi Abba ya basa sadakin kin basa yyi hakan yasa ya koma ya xauna xuciyarsa na tafarfasa, he just can't believe this is happening to his daughter, can Abba xauna ya dau wayarsa ya shiga kiran layin Alhaji Ahmad Bulasawa, sai da ya kusa katsewa ya daga, bayan sun gaisa Abba ya d'an yi shiru sai kuma a nutse ya shiga tambayar Bulasawa dalilin da yasa xa su yi masu abinda suka yi, Alhaji Ahmad Bulasawa dake sauraronsa keenly yace "I really don't get you Alhaji, me ke faruwa, anyi wani abu ne??" Mamaki ne ya cika Abba jin abinda Bulasawa ke cewa, bbu bata lkci ya shiga yi masa bayanin ynda suka yi da Sadeeq yanxun nan, cikin daga murya Bulasawa yace "He is seriously stupid, wato abinda ya xo yace maku kenan, to wllh ko ya ki ko ya so aure ba fashi, my reputation is above everything, ana saukowa masallaci dama daurin aure na nan bbu fashi in sha Allah, till we meet there...." Bai jira cewar Abba ba ya katse wayar, Abba ya kalli Daddy don wayar a hands free ya sa, Daddy ya girgixa kai yana murmushin karfin hali yace "I will never give out my daughters hand in marriage to that son of him, tunda har da kansa ya nuna baya auren that's the end, ba neman kai nake da Imaan ba, don't forget she is all I have got, da a cutar min ita gwara an cuceni ko wani irin cuta ne kuwa, we are returning their pride price and everything immediately, Allah ya hada kowa da rabonsa na alkhairi, Allah yayi mata xabi na gari, bak'i da suka xo from far don taya ni farin ciki xan sallamesu ana saukowa masallaci in sanar masu bbu auren kuma, and I will forever be grateful coz they are all here bcos of my only child, in sha Allah xa mu je a daura auren Yusuf nata kuma Allah ya musanya mata da mafi alkhairi" daga haka daddy ya mike ya nufi kofa, Abba da duk jikinsa yyi sanyi sosai yace "Sadeeq" tsayawa daddy yyi amma bai juyo ba, Abba yace "Don't say anything about this to anybody, not even ur frnds, ka ji abinda nace" Daddy dai bai ce komai ba ya fita parlon kawai, Abba ya jinginar da kai so sad, Yusuf dai ya rasa abun cewa gaba daya he is just shocked, can Abba ya kallesa yace "Go nd get set Yusuf, it's almost time, and don't say anything to anybody yet" mikewa Yusuf yyi jiki ba kwari ya fita parlon Abba ya bi sa da kallo. Gida ana ta shagalullukan biki bbu abinda yasan me ke faruwa, Imaan dai tana bedroom dinta baccin da bata yi jiya ba duk ya dameta, daga karshe ta kwanta ta dinga bacci, bbu wanda ya tasheta cikin mutanen dake dakin don da ganin yanda take baccin ma kasan gaba daya she is restless sai juye juye take. Abba ya dau sadakin da su Bulasawa suka kawo ya tafi gidan da kansa don mayar masu don sosai ya gamsu da abinda d'an uwansa yace na cewar bbu xancen aure kuma tunda Sadeeq din ya fito da kansa ya nuna ya hakura to gwara kowa ma ya hakura ko don gudun kada ya jefa Imaan cikin wani hali, kuma hakan shine abu na karshe da xai so ma only child din d'an uwansa, ko kadan Bulasawa bai ji dadin kudin da Abba ya maido ba don kin karba yyi, Abba yayi masa bayani a nutse yanda xai fahimce me yasa suka yi haka ya kuma nuna masa dole su yi hakan don ceto imaan, ba irin kiran da Bulasawa bai ma Sadeeq a waya ba amma ya ki dagawa, Abba na murmushi yace "Toh kaga Alhaji, kawai Allah yyi masu xabi na gari, tunda kaga haka auren ba alkhairi bane garesu" Bulasawa dai ya kasa cewa komai amma gaba daya shi ma ransa ya sosu, Abba yyi masa sallama daga karshe ya bar parlon nasa bayan ya sanar masa xuwa gobe ko jibi xa a maido masu lefe, shi dai Bulasawa har Abba ya fita bai iya yace komai ba, can ya dau wayarsa ya shiga Kiran mahaifiyar Sadeeq, tana dagawa strictly yace "ki sameni parlona ynxu, kuma duk inda Abba yake I want him immediately, in sha Allahu kuma baxai kwanan min a gida ba yau, and he is returning all my asset that is with him today, I have nothing to do with him any longer" Bai jira cewarta ba ya katse wayarsa. Karfe daya saura Abba suka wuce masallaci tare da frnds dinsa da kawu Bala, sae kawu Audu, bayan ya samu waje yyi parking ya kira Daddy don ya ji yana iya, daddy ya sanar masa yana hanyar xuwa mosque..... Ana sakkowa masallaci aka daura auren Yusuf da Hafsat a kan sadaki dubu dari biyu, auren da jama'ah da dama suka shaida, sae kuma daurin aure na biyu da ake jiran waliyyan ango amma shiruu, wanda hakan yasa aka fara dago kila babu auren ne tun kafin su Abba su sanar da hakan, Abba na kallon daddy dake kusa da shi murya can kasa yace "Abubakar xan daura ma 'ya ta aure yanxu, auren da ina da tabbacin kowa xai yi alfahari da shi in sha Allah, ko ba ynxu ba kuwa, da raina baxan ta6a yarda ka ji kunya a idon duniya ba, kuma ikon da nake da shi a kan Imaan yasa xan daura mata auren huce takaici duk da banda ni da kai da Yusuf sai Bala bbu wanda yasan abinda ake ciki" Daddy dai sai kallonsa yake don tun idar da sllh ya ki cewa komai, Abba yace "Ka je a kai ne waliyyin ango, Bala kuma dama shine waliyyin amarya..." Yana fadin haka ya fiddo kudi a aljihunsa ya mika ma Daddy yace "This is 200k, sadakin da xaka bada...." Abba na fadin haka ya koma gun su kawu Bala da abokansa, ko kadan daddy bai yi welcoming idea din Abba ba, kwata kwata bai son ma imaan dole, bai son tashin hankalinta ya xama biyu, na rashin masoyi ga kuma aure without her consent, gashi bai san da wa Abba xai hadata ba idan kuma yace xai yi magana Abba sai yaga kamar ya nuna masa bashi da iko da imaan, gaba daya he was just confuse haka ya tafi dai don yin ynda Abba yace, Daddy bai taba xaton sunan da yaji an kira na angon ana daura auren, haka ya dinga kallon Abba ko kiftawa bbu, Yusuf kansa was more than shock ya kasa daina kallon iyayen nasa, can ya lumshe ido ya bude xuciyarsa na bugawa.... Abba ya sakar ma Daddy cool smile ganin kallon da yake masa, maimakon Daddy ya mayar masa sai ya dauke kai kawai. daga karshe dai Yusuf fita yyi to avoid gaisawa da frnds don gaba daya shock ya xame masa biyu..... Tun bayan call da Mariya tayi answering a dakin Imaan yanayinta ya sauya gaba daya, tafi minti biyu tsaye har sannan wayar na hannunta, Maimoon dake diban ma Imaan dake xaune saman darduma ta idar da sllh abinci a plate ta kalleta ganin ko motsin kirki bata yi tace "Lafiya Mariya" Mariya bata yarda ta kalli Maimoon ba sbda hawayen da ya kawo idonta, Maryam ta ajiye dankunnen da take kokarin sakawa ita ma tana kallon Mariya tace "Hope all is well dear?" Fita Mariya tayi daga dakin da sauri sai a sannan ta fashe da wani kuka, gaba daya suka bi ta da kallon mamaki, Imaan ta ji gabanta yyi mugun faduwa ta mike daga saman darduman, Maimoon ta mike ta bi bayan Mariya hankali tashe, Maryam ma ta bi bayansu, Imaan ta kalli agogo dake nuna biyu da 'yan mintuna sannan ta sauke idonta a hankali tana karanto addu'a a ranta ko xata samu natsuwa daga bugawan da xuciyarta ke yi, wayarta ta dauko tana dubawa ko xata ga even if it's text from Sadeeq na sanar mata cewar an daura masu aure amma bata go komai ba, ta xauna gefen gado tana goge hawayen dake xubo mata. A hanya Daddy na kallon Abba dake driving xa su koma gida yace "Barrister I don't think what u did was a way a out, ya kake son yyi da mata biyu? A lkci daya kawai" Abba dai bai ce komai ba sai driving yake a nutse, kawu Bala dake cikin motar yace "Gaskiya ne, kada a 6ata daya goma bata gyaru ba, sannan kai baka yi shawara da kowa ba Ahmad" Abba yace "I did what I think is best brothers, da d'an uwana ya ji kunya gwara nayi koma mene, we will sort everything out right daga baya in sha Allah," A haka har suka iso gida babu wanda ya sake cewa komai. Rabon abinci Umma suke yi amma gaba daya ta kasa kunnuwa ta xuba idanu tana jiran dawowarsu Abba da xancen bbu daurin auren Imaan, Safeenah dake hada uban salad sai taunar cingam take ita ma dai tana jiran news, irin cakarewar da tayi kai kace ita ce amaryar, tun sassafe dama ta iso gidan ana ta aiki da ita duk da ta bar Mujaheed yana headache tun cikin dare bata ma san ko xai je daurin auren ba, Umma na ganin shigowarsu Abba duk da ba ita ce mai girki ranan ba haka ta bi bayansa tana masa sannu da xuwa da fara'a tana cewa Allah yasa an daura a sa'a Allah kuma ya bada xaman lafiya, a takaice ya amsa da Ameen, tace "bari in kai maku abinci parlor" ganin mood dinsu gaba daya daga shi har Daddy har ma da kawu Bala taji kamar tayi tsalle don murna, da dukkan alamu dae tayi nasara, Abba na kallon Daddy da ya nufi part dinsa walking like the gentleman he is yace "Sadeeq" juyowa Daddy yyi, Abba yace "Mu tafi can parlona for lunch..." Daddy bai masa musu ba ya dawo suka wuce parlon Abba, Ammi na compound ita ma amma tun shigowarsu ta sha jinin jikinta ganin yanayin Abban Imaan da kawu Bala kai kana ganinsu kasan da matsala don haka bai boyu a fuskarsu ba, Abba ma ne kadai ke d'an yake, abinci iri iri da aka yi Umma ta dinga dire masu a parlor tana cewa "Allah ubangiji ya nuna mana na yan baya, Allah ya basu xaman lafiya gaba daya yasa anyi a sa'a" Babu wanda ya tanka ta a parlon har ta fita tana murmushi sai dai bata ji dadin kin cewa komai da suka yi ba, gashi gaba daya ta hana yan uwanta maxa xuwa daurin aure balle ta kirasu taji yanda aka yi gun daurin auren, fitowa tsakar gida tayi tana hangen inda xata ga Yusuf ko xata d'an samu labari ganin frnds dinsa na ta shigowa compound din... Abba yayi breaking din silence din parlonsa yana kallon daddy da ya jinginar da kansa da kujera yyi nisa tunanin da yake, yace "Naga kamar hankalin ka bai kwanta gaba daya da auren nan da aka daura ba ko Sadeeq?" Kallonsa daddy yyi yace "Not at all, ina dai mamakin al'amarin ne, sannan am hoping this shouldn't be a big blow to my daughter, you know her condition.... Bana son wani abu ya sameta coz baxan iya dauka ba" Abba ya dafe kansa shi ma yana tunanin ta inda xa su fara fasa news din nan wa mutanen gida.... Mama Hadiza ce xaune parlon Abba tare da yayyinta bayan kiran da kawu Bala yyi mata a waya, kai kana ganinta xaka hango tashin hankalin da ke fuskarta karara, lkci daya ta shiga furta Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, Daddy dai kansa na jingine da kujera, Abba ya girgixa kai yace "Abinda ya faru kenan Hadiza, mu ma haka lamarin ya xo mana" Hawaye ya kawo idon Mama Hadiza tausayin Daddy ya cikata, hakan bai kamaci only child dinsa ba, to ko ya ita kuma Ammi xata dau xancen balle ita Imaan din gaba daya, Hawaye ta dinga yi sosai tace "Allah ya isa tsakaninmu da shi, ya cuce kansa ba mu, Allah ya saka ma Imaan..." Abba ya d'an yi murmushi ya ciro wayarsa a aljihu yyi dialing number Mujaheed don sure bai gansa gun daurin aure ba, sai da ya kirasa sau biyu sannan ya daga, Abba ya amsa sallaman da yyi yace "Ban gan ka gun daurin aure ba why?" Mujaheed dake kwance ya mike xaune da sauri yana kallon agogo ganin time cikin sanyin murya yace "I slept off Abba, kiranka ne ya tashe ni ban san lkci ya wuce haka ba, har an daura kenan?" A takaice Abba yace "A'a ana jiran ka, I want to see you home now my frnd..." Mujaheed ya gyada masa kai ya kasa cewa komai har Abba ya katse wayar, hade kai yyi da gado trying hard to control himself... Aunty ce ta fara shigowa parlon Abba sannan Ammi ta dalilin kiran da Abba yyi mata ta wayarta wai su taho tare da Ammi, Kallonsu ta dinga yi bayan ta shigo parlon, Mama Hadiza dai kanta na kasa ta ci kuka har ta gode Allah, Ammi ma ta dinga kallonsu lkci daya taji gabanta ya fadi ta xauna kasa a hankali jin kafafuwanta sun kasa daukarta, Aunty ta xauna ita ma cike da karfin hali tace "In ji dai lafiya Abba?" A takaice Abba yace "Lafiya lau" Kawu Bala yace "Lafiyar kenan Amina..." Bude kofa aka yi Umma ta shigo ita ma ta dalilin kiranta da Abba yyi, ganinsu Ammi da Aunty, da Mama Hadiza a parlor kawai taji kamar ta saki guda mai xakiii, rumors da ake tayi tsakar gida ya tabbata kenan, Ta xauna da mamaki fuskarta tace "Lafiya kuwa Alhaji, me ya faru?" Ko rufe baki bata yi ba Yusuf ya shigo parlon tare da Inna da ta cakare cikin super abunta an daura dankwali sai xuba kamshi take ta daura mayafi a kan dankwalin, tana murmushi baki har kunne tace "Toh Allah ubangiji dai yasa an daura a sa'a Allah ya kauda idon makiya, ya kuma sa gidan xamanta ne, ku kuma Allah maku albarka ya baku lada" Kawu Bala ne ya amsa da Ameen kansa a kasa, shi dai daddy kansa na jingine da kujera, inna ta nemi kujera ta xauna tace "Toh wani shawarar kuma xa ayi yanxu aka tara mu a nan, ga dai bak'i can na baro" Abba yayi murmushin karfin hali yace "Mujaheed muke jira Inna" Inna tace "Ae dole, shi ne ubanta na hudu a nan ai...." Bude kofa aka yi sai ga Mujaheed ya shigo parlon sanye da shadda fari kal sai walkiya yake, duk suka dinga kallonsa ya nemi gefen Yusuf da kansa ke kasa ya xauna ya gaishe da iyayen nasa gaba daya da ladabi duk suka amsa, Abba ya kalli Aunty a hankali yace "Go and get Imaan immediately" Mikewa Aunty tayi ta fita ita gaba daya ta gama shan jinin jikinta don gani take ba alkhairi yasa aka tara su parlor ba, ba alkhairi xa su ji ba. Aunty na rike da hannun Imaan da ke lullube cikin mayafi suka shigo parlon Abba, ta xaunar da ita gefenta, imaan bata iya ta dago ba balle ta ga mutanen dake cikin parlon gabanta dai sae faduwa yake, Umma dai har ta fara lissafin nawa xata kai ma mutumin nan kyauta don nuna masa farin cikinta, gaba daya ta kasa boye how happy she is ah wajen duk da ynda ta dinga dakewa, tunda Imaan suka shigo da Aunty Mujaheed ke kallonta ko kiftawa babu, Abba ya bude wajen da addu'a sannan a hankali yace "Bbu amfanin tsaya jan xance ko wani boye boye, kuma ina son kowa a nan ya dau abinda ya faru yau a matsayin kaddara wanda aka ce ta riga fata, mu ma ba haka muka so ba, kowa ma ba haka xai so ba, sai dai kawai mu kara gode ma Allah don shi ya san dai dai, a takaice dai bbu xancen auren Fatima da yaron nan Sadeeq yanxu..." Ba sai na fadi irin girgixan da mutanen dake xaune parlon suka yi ba a lkcn, ciki kuwa har da Umma da ta dinga salati tana xaro ido tace "Babu aure Kuma, bbu aure fa kace Alhaji, a kan wani dalili xa a fasa aure gashi mun tara jama'ah ta ko ina, me ke faruwa don know" Inna dai gwalo idanuwa tayi ta mike tana kallonsu Abba jikinta na rawa kamar maxari tace "Mutuwa Sadeeq din yyi Ahmadu?" Imaan ta fada jikin Aunty ta fashe da wani kuka mai ban tausayi, Ammi kam bata iya ta daga kanta ba, nan ko ita ma hawayen take, Aunty dake hawayen ita ma tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, me ke faruwa Alhaji" Yusuf bai iya ya kalli mutanen parlon ba duk jikinsa yyi sanyi ba kadan ba, Mujaheed ya dinga kallon Abba ko kiftawa bbu xuciyarsa na bugawa jin abinda yace, kawu Bala yyi kasa da murya yace "Duk ku yi hakuri, we never saw this coming, and we are in it all together, komai ya samu bawa a duniya dama rubutattce ne, kuma bbu wanda ya isa ya kauce ma kaddararsa, wannan yaro Sadeeq dai da kansa ya xo daxu ya nuna ya fasa auren yar mu, tuni kuma mun maida masu sadakin su lefe kuma ko xuwa anjima in sha Allah xa a mayar, Allah yasa hakan ne mafi alkhairi ga dukkanmu gaba daya...." Inna ta rushe da wani kuka da tsorata mutanen parlon tace "To kuwa yanxun nan xan tafi in nemo gidan Bulasawa in ci ubansa da d'an nasa, Allah ya tsine masu albarka, Allah ya tarwatsa su, Allah ya isa tsakanina da su, Allah yyi yaga_yaga da dukiyar nan tasu ta sata, shegu barayi, mu xa su kunyata a idon duniya ga bak'i mun tara ta ko ins, to in sha Allahu kotu ce xata raba mu da matsiyatan, Shari'a ce mai girma xa mu yi tun a duniya kafin mu tafi gaban Ubangijin mu, yau xan tafi in shigar da kara a kotun Habuja...." Abba yace "Don Allah ki sauraremu Inna, dama an taba aure dole?? bbu ruwan ki da su balle aje wani shari'a kawai mu sa a ranmu fasa auren nan shine mafi alkhairi ga 'yar mu, kuma basu kunyata mu ba don bamu bar masallaci ba sai da na tabbatar na fitar da d'an uwana kunya na daura ma 'yar sa aure da nawa d'an da nake da iko da...." lkci daya gaba daya mutanen parlon suka daga kai suna kallon Abba with full shock, ko allura ya fadi a lkcn sai kaji karansa, Imaan taji kamar numfashinta na mata gardama ta dinga kallon Abba xuciyarta na wani bugawan da bai ta6a mata ba, Umma ta hadiye abu da kyar tana kallon Yusuf da kansa dai ke kasa, ji tayi wani xufa na keto mata don wannan shine anyi ba ayi ba, yanxu Yusuf aka makala ma yarinyar nan, Mujaheed dai sai kallon Abba yake xuciyarsa kamar xai fashe sabida yanda yake harbawa, Abba ya mike yana kallon Inna da ta cire mayafin kanta tana kikkifta ido tana kallonsa, yyi kasa da murya yace "Na hada auren Imaan da Mujaheed yau, saboda ina da yakinin xai ma fi Sadeeq din rike min 'ya ta da amana...." *Table_shaker/Media shaker* 🙄✍🏻 *Imaan isn't for free* it's 300 via Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah Then u show ur evidence of payment via my WhatsApp number 07087865788