Copied By HAYATU BABA ZUBAIRU (admin Arewa hausa novels Novels villa Duniyan novels Hayat hausa novels Hausa novels and fashion And Cool novel, makeup and cooking) WHATSAPP NO: +2347039625239 ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠ Page 1-2 By Gentle Lady💃🏽 Dasunan Allah mai rahma maijinkai"" dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah madaukakin sarki maikowa mai komai ina kara godiya ga Allah subhanahu wata ala "" Wanda yabani ikon fara wannan labarin Allah yasa jama a zasu amfana da fadakar wardake cikinsa Hakika komai kaga yasamu bawa mukaddarine daga Allah Amman kuma akwai sanadi wannan labarin kirkirarren labarine nayishi domin tsokaci dawadansu abubuwa dasuke faruwa acikin al umma"" Wacce wannan labarin yaxo daidai darayuwarta saita tuba tadaina domin ganin makomar Wanda yake kwatankwacin irin halintaa Allah yasa mudace Ameen Wannan labarin narubutashine ra ayin kaina danhaka Wanda yaji zai iyah karantawa banhanashiba saidai kuma akiyaye karwani ya sarrafamun shitawata hanyaa idan kunne yaji gangar jiki tatsirah *BISMILLAH* *********************** Gabadaya unguwar cinkushe take da manyan motoci sai kaikawo sukeyi alamu sun nuna wani mihimnin buki akeyi na wani kasurgumin maikudii Dan la akari da yawan motocin dasuketa karakaina hakazalika masu tsadar gaske kaima kasan ba bikin"" fukara"u bane Bakin kofar gidan tacika makill da maroka dakuma masu kidaa"" ahakan nasamu tattakawa zuwa kofar gidan duk da dakyar nasamu nakai wajen asheni banga jama a ba dankuwa cikin gidan tamkar anabikin nadin sarautane"" Sai rarraba ido nakeyi domin samun hanyar shiga wannan katafaren gidan ginane namusamman maihawa hudu anyimasa fentiii da farin fentiii maishegen kyau da shekiii wannan gidan kusan yafi kowanne gida kyau dakuma tsari gabadaya ya haskaka unguwar anayiwa gidan nan lakabida farin gidaa!! Tofa Allah yasa abunda yakecikinsafarine🠽򢠊 Kutsa kaina nayi Cikin gidan kofar shigama abar adubace""nagama zagayena nikam banga alamar matar gidan ba"" dankuwa irin wannan gidan yakamata ace matar gidan ta banbantaa dayanbukiii ajikinta kadai za agane"" Nayi zugum inabinsu dakallo nace tomezaihana insaurari firarsu watakil nagane matar gidan aciki🤔 wannna shawarar nayarda da itah nafarabi lungu dasako ina saurare abun takaici abun bakinciki duk inda nawulga zancensu kusan dayane kishiyaaa!!!! Waimenene illar kishiyane??? Kumata kunada abun mamaki idan mijinku ya aureku yace zaikara aure kuyita fitinaa toyakenan idankuma keza a aura??? Itakuma matarsa taceme??? Yakamata zuwa yanxu mata sugane Susan kalar kishinda zasuyi kuyi koyi da matan Manzon Allah (S A W) suma sunada kishi saidai nasu sunayinsane abisa tsari kowacce tanarigengen wajen kyautata masa domin tasamu matsayi fiye Dana dayar Amman wasufa saboda tsabar bala.i da masifa daga ranarda yasoma maganar kara aure tofa ya ballowa kansa likii zatadaina wanka tabar dafamasa abincii wata hatta gadonta baxata barshi yakwantaba dazaran yace yimun kaza tace bazanyiba kajecen wajen amaryarka taimaka tabar yayanta acikin wahala waifa a irintata wautar waita naso tazubawa mijin haushine shikuwa dayafita iyawa saiyabuge iskanta yayima dadai duniya kamarma baisan da zamantaba sai idan tayi masifar tagababuci kuma biki yanata karatowa sai afara yangyare gyare waidaga bayakenan sadaka da bajawara bayan kinzubarda girmanki kimarki darajarki Bari nabaku wani sirri wlh idan mijinki zaiyi aure kika kwantarda hankalinki zakici arziki komai kikeso zaiyimaki domin yataushi zuciyarki kuma zai rika tambayarki menene kikeso haka zalika komai zaiyiwa amaryar zairika neman sha wararki"" sabanin idan kikasoma fitina zaiyibanza dake duk wuyartadai kece akasa bazaki hanashi auren ba Saikiyi ba1 ba 2. Darajarki dayake gani kinbata bazaisake yarda dakeba kuma koda amaryar tashigo gidan akatada fitina kodakuwa kece mai gaskiya bazai yardaba zaice aiyaga take takenki tunkamin yayi aure kiketa fitina tosaidai kiyi abunda zakiyi matadai matar sace matsayinku daya awajesa uwargida kinga mutuncinki yaragu Idan kikacigaba da fitina karshenta yasakeki yazauna da amaryarsa wagari yawaya???? Hakan yana faruwa sosai acikin al.umma Iyayena mata iyayen gobe mukula mukiyaye kishii ba haukabane!!! Nafara biyar lungu dasako cen saman hawa na uku nayi katari da matar gidan "" sosai nafirgita daganinta sam bazaka taba cewa matar gidan bace"" irin matan nan ne wadan da mazajensu suke dakudi amman idan kagansu bazaka siyesu kwandalaba duk kayanda suke siyamasu basa sakawa idan kagansu mai aikinsuma tafisu daraja amman fa idan zasuje gidan bukii kokuwa zasuje unguwa zakadauka basason taka kasa saboda tsabar tsafta"" Abokananta dasuke gefenta dayar tace wai lubabatu mezaihana kitashi kiyi wanka gidan nanfa yanbiki sunfara cikashi kosokike araina class nakii Wacce take gefenta nadama tace hajiya larai kibarta hakan mana"" dame zataji dakishiyarda akai mata kokuma da kwachakwaimar kwalliya?? Kinsan Allah danice kotaron biki bazanyiba Wata tace habadai hajiya larai aiyanzu andaina wannan yayin idan za akawomaka kishiya kahana kanka jindadin rayuwa yanxu kissa akeyi kikwantarda kai tamkar mumina ni wlh mijina yayi aure saina gasawa amaryar gyada ahannunta Suka kwashe da dariya haryanzu uwargidan uwar iko batayi maganaba""" Larai tace hajiya sadiya kenan ashe wacce tsautsayi yasaka tashigo gonarki zatafi gwammacewa kwana akabarintaa" suka sake shekewa da dariya"" amman banda itah"" Haba kukuwa banda abinku ai kishiya abokiyar zamace menene abunkishin??? Abunda akasaba bakifa badainawa za ayiba nisam banajin kodar akan auren nan Hajia lubabatu ce mai wannan maganar"" Hajia larai tarike haba lallai hajiya kodayake wannan bashine nafarkoba bakyada jinkomai nikam wlh bazan sakewa mijina fuskaba dahar zaiyi sha awar karawani auren"" tirkashi ranarkuwa dahakan tafaru wlh sai yayi zaton aturu aka kwantoni dan zankoma masa mahaukaciyar karfi dayajii Wannan karon harda hajiya lubabatu wajen dariya wata matashiyar budurwace tabude kofarda sallama""" sukabita dakallo babu wanda ya amsa tafara kallon mutanen dasuke cikin dakin daga bisani tadauke kanta kamar taga kashi Hajiya lubabatu ce ta daka mata tsawa ke wacce irin shashashar yarinyace labila???? Zakishigo wamutane daki haka bakiganin bakine dani??? Baki tatabe nagansu mana mom kuma ainayi sallama "" takai karshen maganar tanasake wurgamasu mugun kallo ta murguda bakiii Kinyi sallama gidanwa mu kuramene dabamujiba"" ta kwabe fuska to tayazakuji bayan kuna tazuba shegen surutu wanda bazai kareku dakomai ba"" Ido lubabatu tazaro sukam su hajia larai inda sabo yaci acesun saba dahalin labeela"" tace labila waiyaushe kikazama tsagera nifa mahaifiyarkice kinamun magana tarashin da a Tasake mere baki"" tacee malamai niku gyara zanduba jakata "" tayi maganar tana rike kunkumi afusace hajia lubabatu tasauko daniyar dukanta su hajiya sadiya sukariiketa haba hajia baidace kidaketaba ai labila karamar yarinyace kuruciya ce take damunta Kotakansu batabiba tahauduba jakarta"" tadauko sannan takallesu daibayan daya tace naji kuruciya tana damuna amman karani saudubu daku sakarkarun mataa mstw tsaki taja tafita tabar dakin Gabadaya dakin yayi tsit bakajin motsin komai saina saukewar ajiyar zuciyarasu" labila karamar yarinya amman kullum tasamesu agidan saita soka masu miyagun maganganu Dasauri tasauko kasan tana rike dajakarta"" sai kutsawa takeyi cikin taron mutane ranta yayi matukar kuna bataso mahaifiyarta tana hulda da wadan nan matan saboda dukansu babu Allah azuciyarsu amman mahaifiyarta batada wasu shakikan abokai bayansu Wayarta tajawo takamo wata nomber tadanna kirah babu jimawa akadauka"" tayi sallama ya amsa dad dan Allah katuro driver yamiyar dani bazan iyah zama anandinba!! Ajiyar zuciya yasaukar yace saboda menene labila bazakijirah akawo antyn takiba cikin sauri tagirgiza kai no dady"" dagabaya zandawo inganta yanzu akwai muhimmancin tafiyar tawa gobe munada harda a islamiyya"" amman inshaa Allah idan komai ya daidaita zandawo naga mom din kafin lokacin tazama yargida da murmushi afuskarta tafurta hakan shima murmushi yayi badamuwa labelaa yanzun bari nakirashi yazo amman nayi kewarki yata gashi zaki tafii amman bamudan zantaba"' Tashafo gefen fuskarta bakomai dady zansake zuwa saimuyi firanko?? Yace yauwa yata kikasance cikin amincin Allah Tasaki sassanyan murmushi tace kaima haka"" inasonka babana yace nima inasonkii tace bye yace ok bye taciro wayar akunnenta takuramata ido Allah sarki babana"" Allah. Yasa kayi dacen mata Allah yasa daka wannan auren kasamu kwanciyar hankali wasu sirarun hawayene suka sauko mata tasa gefen mayafinta tashare sake matsawa tayi saboda cinkoson mutane ga shi ankusa la asar"" batawani jimaba driver yazo bayan sungaisa tashige motar suka kama hanyar kano Aisha✍🏼 ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠ Page 3-4 By Gentle lady💃🏽 Sai bayan fitar" labila sannan hajiya lubabatu tasamu tashiga wanka ganin duk jikin kawayen nata yayi sanyi da maganganun da labilar tafadamasu yarinya tamkar banice nahaifeta ba sam bataganin mutuncina Tayi kwabaa Batajima dashiga wankaba tafito tasheka kwalliya tamkar wacce zataje gasar sarauniyar kyau" ta chanchade cikin wani tsadadden bugaggen less dan ubansu akalla kudinsa zasukai dubu dari da hamsin"" Tasaka sarkar diamond hannunta yasha awarwaraye na gwal"" nantake tasoma shekii tashi sukayi dukansu suka fara zaga gidan duk indasuka wurga sai anjinjinawa kwalliyarta nikuwa araina nace wato yangulma kikewa kwalliya illai kuwa kwalliya tabiya kudin sabulu dankuwa tayankesu kowacce takoma gidansu tana Allahummar zukuni"" Wani abun saigidan manya bakuga yanda akasoma fitowa dakayan ciye ciyeba bikin gidan masu kudi ko ba agayyacekaba kaje kodakuwa ba asakarmaka fuskaba kakwaso gara"" Dankuwa yanda akacika gidan kaima dagani kasan wadansu abincin kawaine yakaisu "" babujimawa akafara fitoda dakwalen kajiii dakuma babba kakkun raguna masu maiko"" anyimasu gashi Na musamman sunsha shafen barkono saizubarda mai sukeyi saikuma lemuna namanyan mutane wanidinma bantaba ganin irinshiba Kowa kaganshi rabonsa yake yaga"" masu DJ ne sukafara sakin kidaa bayan suncika tunbinsu""" hajiya lubabatu ce tafara takarawa cikin murna kaikace ba itah za ayiwa kishiyaba babuwanda bata burgeba wasuma sunata rokon Allah yabasu uwargida maihalinta Sam batadauki kishi abakin komaiba Kai ranarfa tasha rawa nikam nace jikinki zaiyi ciwo kuwa""duk wannan bidirinda akeyi banga ma mallakin gidanba"" Yinin ranarfa sunchashe son ransu DJ yakwashi kudii wadanda akaita masu likidasu kasan biki na kusoshin yan duniya wadanda sukarika Shigar hajiya lubabu goma kowacce shigarkuma saiwanda yaganie komai kuma kalar kayan" anzuba hotona"" magrib tana kawojiki kowa yafara haramar barin gidan"" daki suka sake kowama"" suna nan kowadai saifadin albarkacin bakinsa yakeyi Karfe takwas mukafarajin dirar motocin amaryaa"" sunata rangada gudaa"" akashigo da itah"" zuwa bangaren uwargida sukashiga da sallama ta amsa dasakin fuska marabanku lale marhabin kuzazzauna mana"" Daga kawayenta harmasu kawo Amarya bakisake suke kallonta sambatada bakinciki taja hannun amaryar tace zo Kanwata kizauna nan"" cikin jinkunya"" tazauna kanta yanakasa ayanda akebata labarin matarsa babu ruwanta ashema tafiyanda akabata labari"" Take tamike tafara jidomasu kayan makulashe dakuma kayan sha"" da gasassun naman kajie"" bayan sungaisa sukace ga amanar kanwarkinan munkawo maki Duk dakowa yana shaidunki bakida wata illah Dan Allah kiyi hakuri dahalin kuruciyarta dan kingirmeta nesa bakusaba idan tayi badaidaiba kiyimata fada"" Tayi murmushi aibakomai abokin zama dadine dashi tadafa kafadarta"" Kanwata nandin kidauka gidane komai yashigemaki duhu karkiji shakkar komai kisanardani nikuma zanwayarmaki dakai Allah yasa nandin gidan zamankine Allah kuma yasa ace karada akayi Allah yabamu zaman lafiya"" gabadaya aka amsa da amin"" Mikewa sukayi tace yabazaku taba koda ruwabane ai anzama daya nibazanji dadi idankuka kicin komaiba nima idan nazowajenku tareda Kanwata aibazakuji dadiba idan nakishan koda ruwane Sukace tayi hakuri akoshe suke ganin tamatsa yasaka sukadan kurba lemun"" tareda itah akafita zuwa bangaren Amarya """ harkuryar dakin tazaunarda itah yanganin daki Duk suncika dakin"" sunfara tabe tabe"" hajiya lubu tasoma miyarmata"" dakayanda akasoma turewa tadade taredasu sannan tayimasu sallama takoma wajen kawayenta indasuma sunsoma haramar komawa gidan mazajensu""" Tahadamasu shatara Na arziki tarakasu kowacce takama hanyar gidanta"" bangarenta takoma"" hawa na uku shine Nata nabiyu na Amarya maigidan shine hawana karshe"" Idanzakije bangarensa Mahayar Na ura zakishiga kidanna zuwa sama bàsàikin wahalda kanki wajen taka matakalaba Tanashiga bangarenta tarage kayan jikinta tahaye saman makeken gadonta tasoma sharar barciii hardà minsharii hankalinta kwancee saijuyi takeyi sànyin Ac yanashigarta tako ina""" Gabadaya gidan anwatse kowayatafi yana yabon lubabatu da kyawawan halayenta"" karfe shadaya motarsa tashigo gidan"" bayan driver yayi fkng yayi saurin fitowa yabudemàsaa kofaa Yafito"" yacewa driver n ina" habu driver dubamun kagani nayita kiran"" wayarsa batashiga labila kuma bata dauki wayarba Yadan gurfana dasaurii yayi hanyar dakinsu yanakwala masa kirah haryasoma barcii yaji anakiransa firgigit yamike yafito dasaurii taresuka koma wajen alhajin"" Aisha✍🏼 ☠ *HATSABIBIN BOKA*☠ Chapter 5 By Gentle Lady💃🏽 Dukawa yayi yace yallabai andawo lafiya?? Qalau habu tundazu nake neman layinka Amman inajinsa akashe"" Ah yallabai wayarne batada chaji wlh" haba habu yanzu duk wadatacciyar wutar nan da ake sakowa kuma ga gen Amman asamu wayarka babu chaji??? Duk kacinye chajin wajen shiriritaccen cheating dakukeyi kaidai koyaushe maganata dakai akan rashin wayane Yasosa kansa yallabai ayi hakuri kuskurene baza asakeba"" murmushi yayi yace hakan kake fada dai kullum"" ya labilar kun isah gidan lafiya ko???? Kai yagyada ah yallabai kafin magrib nihar najuyo tabada sakoma akawo maka"" yana murmushi yace to daukomun"" Dasauri yakoma cikin dakin yadauko key yabude motarda yaje da itah wata katuwar kulace dakuma leda"" yakarba "" Sukai masa saida safe yawuce cikin gidan kaitsaye hawa nahudu yadosa nikuwa ina biye dashi huhuhu ashe banga komaiba saboda wannan yafi sauran kyau nesa bakusaba Komai gashinan gwanin sha awa" tundaga flowers da kujerun dakin da center Capet" green color ne mai haske" sai makeken TV n bango" saikuma babban agogon bango"" Sai fream da ke dauke da ayatul kursiyyu dayan amanarrasulu gudan lakadja akum"" sai wadansu masu addu.o Sosai tsarin yaburgeni"" kularda take hannunsa ya aje yakarasa kuryar dakin"" kayan jikinsa yarage yashiga yawatsa ruwa yafito jallabiya yazura yafeshe jikinsa da turare yafito kular yabuda danbun kaxane"" sai babbar ledar gasassun kajine gashin gida harda diminsu kansa yadafe shisam yama manta bairikowa Amarya kazaba shikullum cikin mantawa yake"" yayi murmushi labilaa kenan"" mikewa yayi yabude fridge yadauko madarar yoghurt yasauko zuwa bangaren hajia lubabatu da sallama yashiga tayi daidai sai kwasar barcinta takeyi"" ledar hannunsa ya aje yakarasa saman gadon yakura mata ido murmushi yayi yashafo fuskarta shikawai yasan abunda yace azuciyarsa ahankali yasoma tashinta ta ture hannunsa cikin alamun mai barcii kuma yanamata dadi yace maman laby kitashi kokinyi sallah??? Cikin barci tace ah nayifa alhaji harkadawo??? Yace gashi kinyi barci bazaki rakani gun kanwar takiba murmushi tayi wlh nagaji alhaji baxan iyah zuwa ko inaba saida safe tasake juya kwanciya Murmushi yasakeyi Yaja bargo yarufemata jikinta yafito zuwa bangaren Amarya Yanashiga daddadan kamshi yadaki hancinsa yalumshe ido sannan yabude ahankali yafurta Alhamdulillahi ala ni imati" Yataka harcikin dakinta tana zaune tsakiyar gado yadine sanye ajikinta "" dashikuma akarufe mata kanta dashi"" Ahankali yataka yazauna saman gadon yayimata sallama ta amsa ahankali"" hannunsa yasaka yadage mayafinda akaimata rufadashi Murmushi tasakarmasa takanne ido daya"" wani dadi yaji yamamayeshi yana tunanin zaihuta sosai ajikin habiba dantunkafin ya aureta yagano macece mai yawan sha awa shine dalilinda yasaka hartarabu damijinta Wanda tafara aura"" Mayafin yasaukar yace Amarya bakya laifi"" koda kinkashe Dan masu gida" tayimasa fari"" da ido"" yasaki fara a tashi muyi sallah mugodewa Allah"" mikewa" tayi daga kan gadon tashiga tayi alwala tafito tasamu yashimpida abar sallah yanagaba yajasu sallah bayan sun idar yagabatar masu da kajin da labiba ta aikomasa dasu kitchen dinta yaje yadauko plate yajuye masu naman yakalleta yace bisimillah cikin jinkunya tace nakoshi Yace wasa kikeyi nasan bakici komaiba hidimar buki nima kaina yunwa nakeji kodai nabaki abakine?? Yayi maganar yana jawota tanarke ajikinsa tashagwabe murya nakoshi my love Yace nifa banyardaba kokadanne saikinci ahakan yadibo yanufo bakinta cikin kissa take karba harsaida yatabbatar takoshi shima yaci yasha madarar"" sannan sukafara wasanni Ganin kasan bazaimasuba sukakoma saman gado yatashi zaikashe masu wutar dakin koda yadawo yasameta sai munsharii takeyi abunyabashi mamaki matuka dagazuwa kashe wuta wane irin barcine zaidaukeka kuma ayanda takeyin barcin kamar tadade dafarashi"" baikawo komai aransaba duk da amatseyake yauyaso more Daren amarcinsa da Habiba jiki asanyaye yaja bargo yarufemata jikinta yamiyarda kayansa"" yakwanta gefenta ido yakuràmatà Kamar maison tunawani Abu"" munshariii takeyi tamkar gurnanin zakii yayita juyi Sam barci yaki daukansa"" haryasoma jantsaki karshedai mikewa yayi yakullemata kofar dakin yakoma bangarensa Aisha✍🏼 ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠ Chapter 6 By Gentle Lady💃🏽 Dashigarsa dakinsa bai tsaya ko inaba sai akan makeken gadonsa "" yazube tamkar gajiyayyen mutum wanda yayi tafiyar yini guda cur batareda ya hadiye kwayar hatsi acikin saba" gabadaya damuwa ta mamaye zuciyarsa Take yafara sake sake acikin ransa" wai me wannan takenufine??? Kowacce matar dazan aurah salonta daban yake itakuma wannan natasalon yaudarar abarci zata fake?? Yayi kwaba bakomai komai daren dadewa aizankaigaci inhar tasan wata aibatasan wataba lallai inkere nayawo zabo nayawo babu shakka saisun hade Inma makircine irin nasu namata zanganota idan yanzu tayi makircin barci saina gani idan darana zatayi hakan"" yayi tsaki maganar banzama yau Allah kadai yasan bururrukan dasuke cikin raina awannan Daren Amman komai yarushe nakoma tamkar wandama baitaba aureba "" ina amfanin dukiyata??? Kansa yadafe Wanda yaji yanayimasa barazana tamkar zairabe gida biyu saigashi yana kuka da idanuwansa hawaye wadansu sunabin wadansu"" Waini saiyaushe zansamu kwanciyar hankali??? Wacce irin rayuwace nakeyi?? Duk irin tarin dukiyarda nakeda itah nakasa samun abunda nakeso saboda duka matan bakin halinsu dayane kowacce zan aura sainaga salon cin amanarta yafigaban kwatance Yashafe dakiku arba in yanata kuka shikadai batareda mai rarrashinshiba daga bisani mararsa tasoma ciwo wanda wannan ciwon kusan yazame masa tamkar ibada yadade agun yana mirgina tareda addua sannu ahankali ciwon yasoma sauka tamkar yanda ruwa suke sauko wadaga sararin samaniya "" yana nan agun bai motsaba saida sanyin alfijir yasoma bugomasa yatashi""alokacin yaji jikinsa yakoma daidai tamkar wani Abu baisameshiba Kaitsaye bandakinsa yashiga yawatsa ruwa sannan yadauro alwala yashinfida abar sallah yafara sallah"" Saida akayi kiran asalatu sannan yasauko da charbinsa ahannu yanufi bangaren lubabatu hawana uku kamar yanda yabarta da dadaren hakan yasameta saidai wannan karon zaninda yakejekinta tuni yakoma gefe tamkarma tunfarko batareda shidin takwantaba""" Bayan under dayake saye ajikinta da tinbir zatakasance gashi tatara taiba sai kirjinta dasuke manya manya kowanne daya yayi girman kofin roba Gefe da gefe nacikinta amurde yake alamar jindadi dakuma Hutu sunkwanta akan lafiyayyar fatar jikinta tamkar irin dika dikan matan yarbawa hakan take Yaduka ahankali yadauki zanen yarufamata ajikinta daga bisani yasoma tashinsa ahankali"" yadade yana tashinsa sannan tabude idonta"" yace tashi kiyi sallah"" murmushi tayi tasake juya kwanciya tace hutunake "" batareda yace komaiba yawuce zuwa bangaren habiba cikin yanmintuna kalilan Na urar tasadashi da bangarenta dakin yashiga tanakwance takama filo tarungume kamar wacce tasamu jariri"" haryanzu lullube take ciikin zanen gadon"" yataka kusa da itah yasoma bubbugarta ahankali yanakiraan sunanta"" tasoma juyi cikin barcinta maidadi tasoma bude idonta ahankali tadorasu akan mijinta tasakarmasa murmushi maikamada tusar jaki"" tabude bakinta daniyar magana tuni yakawarka fuskarsa sakamakon wani mugun doyi dayafito acikin bakinta tamkar gawar mushe ya tunkari kofofin hancinsa" cikin sauri yajuya yayi taku biyu tareda toshe hanchin nasa sakamakon yankayan cikinsa dayaji suna hautsinawa cikin sauri yace sauri nake kitashi kiyi sallah"" baijirah Jin amsarda zatabashiba yayi waje haryacin tuntube Sam habiba batakawo komai arantaba saitadauki hakan amatsayin yanasaurine karyarasa jam i saboda falalarda kecikin sallar asubah acikin jam"i Shiru tayi nawani lokacin tana tunanin daren jiya"" Sam tamanta abunda yafaru tayi iya kokarinta kozata iya tuna abunda yafaru bayan hawansu akan gado damijinta Amman takasa tunawa datamatsà datunani saitaji kanta yasoma ciwo take tayi saurin fatattakar tunanin daga zuciyarta tamike tadaura zani takarasa bayin domintayi wanka Shikuwa dafitarsa yasoma saurii haryana waigen dakinta haryanzu dayan hannunsa yanakan hancinsa yadadeshi kyam yace aransa waiii wannan wane irin warine naji tamkar rubabben mushe"" wannan warin daidai yake da aturmuya kanka acikin shadda wacce taikwana shida arufe itakuwa wannan dawanne kalar mangoge hakorah take amfani dashi kodai rashin wanke bakine??? Idankuwà hakane akwai matsala dankuwa bazan iyah kusan tartaba muddin inajin wannan doyin Dawannan tunanin yasauka kasa yasoma tashin ma aikatan gidan domin wucewa masallaci dama al adarsa kenan bayazuwa masallaci sallar asuba batareda yatada dukan ma aikatan gidanbà wannan dabiar tashi tanamatukàr burge yaran gidan asanadin hakan drivernsa Sunday yakarbi addinin musulunci Wanda yanzu akekiransa da Abdullahi Sosai halin maigidàn nasu yana burgesu basu kadaiba hatta makotansa Dan mutunne Wanda yasan hakkin makotàka sautari idansukàje masallaci inyaga ankusà tàda sallah wani makocinsa baishigoba dakansà yake zuwa ya bugamasa duk da shidinfa maikudine Amman Sam dukiiyarsà batasakashi yazama maigirman kaiba Aisha✍🏼 ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠ Chapter 7 By Gentle Lady💃🏽 Sautari talakawan anguwar suna matukar mamakinsa saidai shi Sam baidauki wai girmankai yadorawa kansaba girmankai Wanda mafiyawan masu kudi suka sakawa ransu" dazaran sunyi kudi zasufara daukar kai Sam sumanta da lokacinda suke fakiransu gabadaya abokanansu nabaya saidai idansuka wulgo cikin mota sudagamasu hannu wanikoma dagahannu bazaiyiba yama manta dayataba zama wata majalisa"" dazaran yaga Wanda yasani talaka saiya saki gilashin motarsa yakauda kai gefe tamkarma baiga mutumen ba Wannan girman Kaine kuma duk Wanda yakedashi yasani yakama hanyar halakarsane saboda abunda kesauran halakarda bawa girman Kaine dagahakan zakafara hassada kanadaukar kanka wata tsiya bakaso wani yayi kudii kamarka kasani ko shaidan abunda yasakashi hassada girman Kaine haryakaishi ga fadawa halaka . Allah yaciremana girman kai dakuma hassada acikin rayuwar mu Ameen"" saida yajirasu dukansu sukayi alwala sannan yawuce suma suka Mara masa baya "" zuwa masallacin unguwar Babu nisa Dan gabangidansa kadan akagina masallacin Ku San babu kwadagar kowa wajen ginin shine yadauki nauyin komai masallacinda aka kawatashi ko acikin manyan unguwanni saikayi dakyar kafin kasamu mai kyansa"" Dan asalin wajen wata tsohuwar ginace akazagaye korufin kwano babu akarosheta akagina wannan masallacin Wanda fankoki da ac kamar suyi magana idan kashiga kamar karka fito sannan gatarin littafai nan idan kanason karantawa"" bayan an idarda sallah"" yakoma gefe yasoma karatu inda sauran ma aikatan wajen sukasoma karatun zuwa adanjima sukafita zuwa wajen aikinsu"" Dai daikun jama ar wajen suka soma fita ahankali haske yanagama wartsakewa shima yatashi yakarasa wajen liman sukai musabaha sannan yafita zuwa gidansa tun a hanya suketa gaisawa da makotansa haryakai gidan dashigarsa yasamu ma aikatan gidan sungama aiki shikawai suke jirah bayan sungaisa yawuce cikin gida sukuma sukawuce Dayake yauranar lahadine babu aiki duk da yakeshidin dankasuwane yanada campani masu yawan gaske Amman yanayin tsarinsa tamkar aikin gomnaty dashi da ma aikatansa Basazuwa aiki asabar da lahadi acewarsa takasance ranar Hutu gakowa saboda idan sukaje takwas nasafe basa tashi sai karfe takwas darabi Ranar lahadi da asabar taxama ranar Hutu kowanne magidanci yafuskanci iyalansa yaji damuwarsu"" idankuma marar aurene yaje wajen budurwarsa idankuma yanada wata lalurah yayi koyayi ziyara"" musamman jumua dan ranar juma.a karfe hudu aketashi Shikuma ranar asabar inhar yashiga gidansa bayafitowa bayan zuwa masallaci yanatare da matansa yakasance lokacinsune komai sukeso kosunada damuwa saisufadamasa duk da kafinsu kwanta kowanne darema suna ganinsa Kaitsaye bangarensa yanufa yasakeyin wanka yakwanta kasancewar barcin jiya Yana nan a idonsa take barci yayi awon gaba dashi Hajiya lubabatu ce tashigo dakin cikin takun kasaita balaifi yautayi kwalliya dass da itah fuskarta saifitarda sihirtaccen murmushi takeyi ahankali tataka zuwa saman gadon taxauna hannu tasaka tanashafo lallausar sumar kansa Wanda takwanta luf gwanin sha awa hakika tana matukar son mijinta dakuma kishinsa fiye da tunanin mai karatu hakaxalika tana mutuwar kaunarsa da begensa fiye da tunanin duk wani mai tunani taja gauron numfashi" atake talulaya wata duniyar daban Sai farkawa yayi yasamu hajia lubabatu tasakashi gaba hannunta yanakan gashin kansa idanuwanta suna kallon saitin drawer yayi kuru yana kallonta daga bisani yasaka hannu yashafo fuskarta tadan zabura sannan tasaki murmushi hannu tasaka tajawo hannunsa daga kan fuskarta tace harkatashi ??? Murmushi yasakeyi akaro nabiyu yace ah tunanin mekikeyi??? Taware ido waini batunani nakeba Yace bayan Wanda nagani"" tayi murmushi ah ah alhaji wai shin inakabar Kanwata??? Tayi saurin kawarda zancen dawannan tambayar"" yace tanadaki tanabarci mana"" Cikin zolaya tace barcin gajiyako nasan halinka basauki jiya bakabarta tahutaba duk da take yarinya batasaba sosaiba Yayi murmushi yace kinfara ko lubabatu yayi kyau inhar nakama ki akoma zakiyi bayani Aransa kuma yace hmm inakikasani saida ta talemun kaza tacinye sannan tasoma barci kamar kasa yayi maganar yana mikewa daga kan gadon yashiga toilet domin watsaruwa Aisha✍🏼 ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠ Chapter 9 By Gentle Lady💃🏽 Bazato kawai saiyafara jin amai"" dasauri yasauko zuwa bayin dakin dagudunsa yasoma kela amai tamkar zai amayarda kayan cikinsa yayi matukar galabaita"" take yazube acikin toilet din yana hakii tamkar wanda yayi gudun tsere da kartii goma"" Tsayin mintuna talatin yana wajen sannu ahankali yasoma samun natsuwa mikewa yayi yasakarwa wajen ruwa yawanke bakinsa sannan yafito kallo daya yamata yadauke kansa wasu hawayene suka sauko akan fuskarsa harzai wuce saikuma yadawo tareda saka hannu ya dade hancinsa zuwa saman gadon" yaja abun rufa yarufe mata jikinta sannan yawuce dasauri Dayake akwai yalwatattun dakuna abangarensa tamkar wani babban gidane ahawan wani bangaren yashiga"" jiki sanyaye yakarasa bayin yayi wanka yadauro alwala domin koda yakwanta bazai iyah barciba Washe garin ranar Sam fuskarsa batada wani walwala dankuwa alal hakika wannan lamarin yasoma kaishi bango yanaji yanagani zai halaka kansa"" ko lunch dasukayi sama sama yaci daga bisani yamasu sallama yawuce ko rakiyar bainemaba dama dai yau rakiyar habibace Dan haryanzu hannunta yake Saida akayi kwanaki uku cur kamar yarda addini yasimfida budurwa sati daya bajawara kwana uku Amman harzuwa wannan lokacin baisamu kwantawa da itah ba"" gashi hargirki yadawo akan hajiya lubabatu"" Dadare suna zaune akan kujerah sunashan kayan itatuwa habiba tana barin gefensa nadama hajiya lubabatu tana barin hagu kokadan ayanzu bayajin warinta koda tabude bakinta"" aransa kuwa yana ayyana damacen muguntane bataso yakusanceta akwai abunda take sakawa ajikinta duk lokacinda tasan zaizo mata""" ahankade yake kallonta Bayan sungama Shane yayi gyaran murya yasoma yimasu nasiha akan zamantakewar aure daga bisani yace kamardai yanda kukasani yaudai kwanana uku dakin Amarya danhaka yau za araba kwana kwana biyu kukeso ayi ko daya daya??? Hajiya lubabatu ce tayi saurin tarar numfashinsa tace maigida nidai kasan banda wata matsala amatsayina na antynta nidai nayafe nawa kwanakin nabaku watadaya kumore amarcinku Jiyayi tamkar yafasa ihu Dasauri yabude baki daniyar yin magana ta dakatàr dashi tahanyar rufe masa baki dahannunta tana girgiza kai cikin murmushi tace karkadamu basaika godemun ba nimaisonkace Inason duk wani farincikin ka ninasan amarcin nan bai ishekaba"" bazan cutuba harcikin raina nabar maku zuwa watadayan saika rabamana kwana Gabadaya jikin habiba yayi sanyi son hajia lubabatu yashiga ranta lalai kowa da irin halinsa bata taba ganin macenda batadau kishiya abakin komaiba kamarta Allah yabarmu tare hajia Al amarin alhaji kuwa sandarewa yayi awajen saboda kaduwa dajin furucin lubabatu anyakuwa tasan masifarda nake fuskanta??? Yanisa aransa batasaniba nasan datasani dabazataso incutuba"" yanda takesona fiye darayuwarta "" kuma haramun ne kasanarda matarka sirrin abunda ketsakaninka da dayar matarka dasaina fadamata"" yaja dogon nunfashi yace shikenan mungode hajiya yanayin yanda yayi maganar kaida ganinta kasan ba cikin dadin rai yayiba""" Basuwani jimaba hajiya lubabatu tayimasu saida safe tawuce bangarenta"" shima hakan yasaka yamike zuwa dakinsa hakama habiba"" sosai yau taraya aranta zatafaranta ran maigidanta domin samun abunda yakeso Bayan tayi wanka tashirya cikin shigar kayan barci farare masu sharara tafeshe jikinta da kalolin turarukka"" kaitsaye bangarensa tanufa Tasameshi yayi shirin kwanciya yana ganinta gabansa yafadiii yaukuma meyakawota alhalin bankirataba ???? Batareda tanemi iso daga gareshiba tayi saurin fadawa jikinsa""" ’’kafin yayi kokarin tureta daga jikinsa hartafara aikamasa dasakonni tako ina""" Takesuka zube akan gadon tunbaya maida martani haryasoma maida mata da martani""" abukamar zaitafi ahakan sannu ahankali yasoma jin doyin tunyana daurewa tareda toshe hancinsa saiyaji abun kamarma karoshi akeyi kusamma doyin yafi nakoyaushe Bashiri yahankadata gefe yamatsa baya dasaurii""" itakuwa alokacin hartayi barci abunta saitasake gyara kwanciya Gefenda take yakuramata ido tamkar maison tunowani abun dagakarshe wanka yashiga koda yadawo baisametà dakinba tafita Tsaki yayi damashi yasan komai takeyi dagangan takeyi kawai danyanason hakkinsa tana nema takasheshi indai Dan wannan ne bazansake nemantaba Darenkuwa daciwon ciki yakwana"" tundaga ranar kullum idan sukatashi don su kwanta"" saikawai yarufe dakinsa kuma koda tabugàmà bazai budeba Amman Sam bayanuna komai idansuna tareda lubabatu ahakan har akacinye watadayan da hajiya tabasu Aisha✍🏼 ☠ *HATSABIBIN BOKA!!* Chapter 8 By Gentle Lady💃🏽 Tabishi da kallo dawani boyayyen murmushi Wanda itah kadaice tasan ma anarsa"" tana nan akan gadon haryafito yana daure da towel Yadauki comb yana taje sumar kansa"" saida tayi luf sannan yadauko turarukka yasoma fesawa ajikinsa"" yafesa akalla turare kala biyar sukahadu sukabada wani kalar kamshi na daban kaisaikace ma aiikatar turarece tayi ambaliya Wata bugaggar shadda ja wacce taji aikin hannu da zare jinin kare maiduhu dinkin tazarcene daidai wandonsa bataja kasaba kamaryanda wandonsa baiwuce idon kafarsaba" Yadauko hukarsa kube maikalar kayansa hatta Zanen hular tamkar tarema aka kerasu"" yadaidaita tsayin hularsa sannan yajuyo wajen hajia lubabatu yasakar mata murmushi yace mujeko dannafarajin yunwa yayi maganar yanashafo cikinsa Batareda tayi maganaba tamike sukajerah zuwa kasa kowannensu fara a kwance akan fuskarsa"" aka idar sa falon kasa yakeyin break saboda masu aikine sukeyin komai shiikuma bayason masu aiki suhau saman sa inhar ba matarsaba babu Wanda yataba shiga saman"" Kaitsaye saman dinner suka nufa yaja kujerah yazauna tadubeshi tace bari nakirah Kanwata ko batareda yakalletaba yace ok" Kaitsaye tasake hawa mahayar zuwa bangaren Habiba"" bakin kofar dakin tatsaya tana kwankwasawa cikin dakin akace waye shigo" taturah kofa habiba tana ganinta tasaki faraa danta shaidata tace Anty kece inakwana Tamayar mata da martanin murmushinta tace lafiya qalau Amarya yakwanan amarci ya kuma bakunta?? Murmushi tayi kawai tadone kanta kasa"" Hajia lubabatu tace hmm kunyata kikeji Amarya nifa antynkice kinga taso muje mukarya nasankema kinajin yunwa"" Batareda tace komaiba tamike hajia lubabatu tanagaba tanabayanta itakuwa saikada mazaunai takeyi kamkar randar ruwansha Harsukakai kan dinner din itah ta gabatar masu da abincin sukaci sukai hamdala sannan suka koma cikin falon suka zauna sukasoma firah Dama ankusa azahar bayan yayo sallah yasake dawowa falon alokacin duk basanan"" baijima daxamaba hajia lubabatu tafito tanaganinsa tawashe baki harkadawo yace ah wlh kusadashi tazauna Yace inakuma habiba??? Tasake murmusawa tace banda abunka alhaji kasan kunya takeji bata sababa nidai nayafe hirar kakoma bangarenta zakufi sakewa kudarji amarcinku Murmushin yake yayi yace hakane kuma kinkawo shawara mai kyau yamike yana gyara tsayuwar rigarsa yayi hanyar mahaya itakuma takoma bangarenta Kofar dakinta yatsaya yana sake sake aransa karshedai kawai yayi kundun bala yaturah kofar tareda sallama tana zaune cikin katon falon tana kallo tadago cikin fara.a ta amsa masa" dannesa da itah yaxauna yana Dari Dari yace kallo kike??? Tace ah kanta yanakasa yace dakyau"" dagahakan baicekomaiba"" saidai yanata satar kallonta takasan ido haryana hadiyar yawu kafin cikar mintuna ashirin yaji baxai iyah dakatarda kansaba cikin kasalarlar murya yakirah sunanta ahankali ta amsa yayimata nuni akan tazo babu musu kuwa tataso Al amaridai anan yasauya yafara aikamata da sakonni dayake yanayi yana kauce hancinsa dankarya shakomasa abunda yafi karfin Tunaninsa tsayin mintuna goma yasunkuceta zuwa kuryar dakin Abun mamaki yana ajeta akan gadon yajitafara wani minshari arazane ya kwalalo ido cikin kaduwa yace barcin kuma???? Waimeke faruwane kodai yarinyar nan aljanun barcine da itah?? Kuma dantsabar shakiyanci ace barcin bayazuwa sai idan nazoda bukatata"??? tsaki yaja yamike akan dagon yafita abunshi zuwa bangarensa Saida akayi la asar yafito da mamaki yasameta cikin falon kasa da itah da wata kawarta"" kallo daya yamasu yadauke Kansa yawuce fuuuu tamkar kububuwa dansosai amaryar nan tasa tasoma batamasa rai jiyajiya dakawota jifa dazun barcitake haikam Amman gashi kawarta tazo tawartsake tamkar batayi barciba Anjima nasan mezanyi Dawannan yakawarda tunanin yakarasa masallaci"" Habiba kam tacika da mamaki duk da bata nunawa kawarta dakwai wani abuba Amman tanacikin damuwa tarasa meke faruwa aduk lokacinda zaitara da itah batakoma sanin meke wakana saidai tafarka taganta itah kadai idan kuma tamatsawa kanta da tuna abunda yafaru saitaji kanta yasoma ciwo Har da dare taresukai dinner sukadan taba firah tayi masu saida" safe tayi bangarenta" batajima datafiyaba hajia lubabatu tamike tayi hamma"" tace nizan kwanta" alhaji saida safe" Shima yamike yace kenan duk kunwatse kunbarni""anan kamar tsinkàkken silifas"" bakomai muje inrakaki" tayi murmushi tayigaba"" yana bayanta saida yarakatà har bangarenta" saida takwanta sannan yarufemata kofa Yakoma bangarensa yayiwanka Yayi shirin kwanciya wannan karon kiranta yayi awaya tasameshi bangarensa""cikin shigar kayan barci masu sharara dukkan halittar jikinta ta bayyana" take Yakama zumudi jikinsa yasoma karkarwà tamkar zakinda yakwana biyar yanajin yunwa aganinku mezaifaru idanyayi arba da abinci Ahankali ta takazuwa wajensa"" babuwani bata lokaci sukafara faranta ranjunansu"" kafin wani lokaci sunkai saman gado kamar almara saigashi tasoma barci Ganin hakan yasa yaji haushi aransa yace kobarcin mutuwane bazai hakurabà saiya Kore kishinsà yanata"" kokarin biyan bukatarsa tasoma gurnani tanabude bakinta wani"" mugun doyi yana fitowa babu shiri yasa hannu daniyar rufemata bakiii yajikamar yataba wasu hakorah zagan zagan"" take Kuma zuciyarsa tasoma tashi " Aisha✍🏼 ☠ *HATSABIBIN BOKA!!* Chapter 10 By Gentle Lady💃🏽 Alokacinne akaraba girki" yakoma hannun lubabatu"" Habiba Sam takasa gane wanne irin aurene tayi gatadai batadawata makusa wacce zatasa namiji yaji baya sonta" batada matsala tabangaren kishiya saidai tabangaren miji"" sosai yakesonta kafin auren ammankuma gashi tunda tashigo gidan komai yadargwaje tarasa gane kuma dalilin yinhakan gashi tanada tsananin bukata zuwa yanzu tarame tafige tafita hayyacinta""" Kwance take cikin falonta kasancewar yauma ranar hutuce yanagida Amman takasa fita domin ganinsa kawai zaisake tasomasa da bukatarta wacce tasan bazata samu maganintaba "" lallai tayarda akwai abunda yajefaruwa da itah cikinta taji yasoma juyawa tafara murkususu"" Tun tana kankujerah hartafado kasaa wata irin kara ta kwallah daidai shigowar hajiya lubabatu tazo kiranta suci abinci dasauri takarasa arude tadagota tana tambayar lafiya kafin tarufe bakinta jinine yasoma zubowa dakarfiii ta gabantaa"" Cikin tashin hankali lubabatu tace habiba dama bakida lafiyane???ina habiba tamatukar galabaita bata iyah kodaga kanta dasauri hajiya lubabatu ta kwantarda itah tafito dasauriii zuwa kasan A firgice tana kuka yana ganinta yamike yana tambayarta lafiya hajia??? Cikin kaduwa yaji meyafaru tace munshiga uku habibace ba lafiya Kafin tarufe bakinta tuni yahaurah saman baimabi takan na urarba tasaman benen yataka tuni hajiya lubabatu tabi bayansa koda suka karasa hartasuma ga jininan yanata malala"" gakuma wata karamar halitta wacce batawuce girma Dan kadan gareba"" take jikinsa yahau rawa duk da abunda yagani Amman hakan baisa yadamuba ya ciccibeta duk dajinin dasauri yasauko kasa hajiya lubabatu tana bayansu sai kuka takeyi Tunkafin yafita yasoma kwalawa driver Kira"" dasauri yafito jinkiran jikinsa yanarawa Dan dagajin kiran yasan ba lafiyaba"" ganinshi damaidakinsa ahannu yasaka yabude masu Mota dama ashirye take"" akasakata taresuka dunguma har hajiya lubabatu zuwa hospital"" emergency akawuce da itah kaitsaye bakin kofa aka dakatar dasu aka hanasu shiga""" Dagashi har hajiya kaikawo sukeyi awajen kowanne kagani kasan yanacikin tashin hankali tsayin awanni biyu likitan yafito dasaurii alhji yatareshi "" saidai yadagamasa hannu yawuce haryana hadawa dagudu"" Zuwacen yadawo yashiga dakin"" ansake shude wasu awannin saigashi yafito Alhaji yatareshi tareda hajiya lubabatu harsuna hadabaki wajen tambayar yamaijikin??? Zufan kansa yashare yace kukwantarda hankalinku insha Allah zatasamu lafiya"" yanzudai muna bukatar jini cikin gaggawa"" kafinma yarufe bakinsa yace muje a auna idan nawa zaiyi"" hakan kuwa akayi saidai jininshi baiyiba Adole akakirah yan uwanta mahaifiyarta "" dakuma yayyunta""" su ukune kowanne akadibi gorah biyu ajikinsa"" take akajonamata anasaka jini jinin yanafita""" Harzuwa dare babuwani haske hakazalika sunkasa tsayarda zubar jinin"" yanda yakezuba zuba banawasaba hakan yasaka sukanemi Karin wani jinin"" duk dayana fita idan ansakamata"" Yan uwanta basuda wadataccen jinin gashi har andibi gorah biyu dagahakan baza sake dibaba"" gashi duka jininta ya tsiyaye"" hajiya lubabatu sai kuka take tace aduba konata zaiyi itakam bataso tarasa kanwarta Likitan yatausaya mata sosai yace saidai hakuri hajiya ba adiban jinin mace"" cikin karaji ta chakumo wuyansa tace inaruwanka jininka konawa Tasakeshi cikin kuka tahada hannuwanta gida biyu Dan Allah doctor kataimaka mana wlh koda zanrasa raina tasanadin dibar jinin nawa"" wlh nayarda Amman banaso kanwata tamutu Jiki asanyaye yagyada kai ganin kowanawajen yazubamasa ido"" take aka auna jininta baidakomai"" akasoma diba anasakawa Habiba"""likitàn yafita mahaifinta dawani kaninsa sukabishi abaya"" zuwa office dinshi"" mahaifintane yasoma tambayarsà meyakedamuñ yarsa??? Yayishiru dagabisani yace barine tayi" cikin kaduwa mahaifinta yace barin lafiya watadaya da aurentafa??? Yajinjinà kai tareda turomasa takarda gabansa yace sakamàko yanuna tanashañ kwayoyin zubarda cikine babisa ka idaba shine yajawomàtà wannan matsalar Kafin yarufe bakinsà alhaji yashigo dasauri yace doctor kataso jinin ya facce kusan taresukà mike dasauri zuwa dakin harsunà hadawa dagudu Sannu ahankali tabude idonta takurawa gadonda hajiya lubabatu take kwance ido sirarun hawaye suka saukomata Take tasoma Kalmar shahada"" idanuwanta sukai sama take Na urah tasoma kara"" daidai shigowar su doctor yakarasa wajentà yayi yan aune aunendà zaiyi yagirgizà kai Yacire abun Karin jinin tareda Na hajiya lubabatu yarufe mata idonta yaja kallen yarufeta"" gabadaya dakin shisuke kallo Dan haryanzu basu fuskanci meyafaruba Yajuyo dakallonsa wajen alhaji yace saidaifa kuyi hakuri Allah yakarbi abarshi"" Daga haka yajuya yafita hajiya lubabatu tasoma kururuwa tana wayyo itah tabani mahaifiyar habiba saman gadon lubabatu takoma tanabata hakuri suka rungume juna sunata kuka""" akarasa Wanda zai rarrashi waniii Tsayin mintuna talatin mahaifin habiba dasauran yan uwa da sukazo dakyar akasamu su hajiya lubabatu sukai shiru Kanin Mahaifiyarta yakalli alhaji yace waimenene musabbabin ciwon nata""??? Kodama tadade batada lafiya??? Ciikin sanyin murya yace shima baisaniba yadaifàdamasu iyah abunda yasani ahakan"" mahaifinta yace sai asamo mota suwuce gida babu wani bata lokaci akadauki gawar zuwa gidan iyayenta"" Aisha✍🏼 ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠ Chapter 11 By Gentle Lady💃🏽 Gabadaya gidan iyayen nata akanufa harda Alhji"" saidai dare yayi Dan lokacin andade dayin sallar isha I"" hakan yasa akaimata wanka aka suturtata" zatayi kwanan keso washe gari sai akaita gidanta na gaskiya Cikin Daren su labila sukasamu labari anasanarda itah tarabka salatiii kukane yakwace mata taruga cikin daki waisaiyaushe mom zatadaina kashewa dad matane??? Meyasa haryanzu nakasa sanardakowa abunda take aikatawa??? Ninasan koda nafadadin babu Wanda zaiyarda dani ganin irin yanda take nunarashin kishi akan matanda yake aurah Ya Allah ka gaggauta tona mata asiri"" wasu hawayene suka sauko akan fuskarta tashare""" tundaga bangaren lubabatu har alhaji babu Wanda ya runtsa acikin Daren sai rarrashinta yakeyi washe gari labila abdulmajed da hajiya da kannen alhaji hafis da kubra suka kamo hanyar kaduna Koda sukashigo kaduna bakwai darabi"" alokacin har anyimata sallah antafi Kaita makwancinta"" su hajiya gidan su habiba aka kaisu sukayiwa iyayenta gaisuwa"" Harda hajiya lubabatu sukaje idanuwanta sunyi suntul saboda kuka kowayaganta saiya tausaya mata"" iyayenta Kansu basuyi kuka kamar yanda tayiba"" labila Kuwa dage take kallonta dankuwa tasan aikintane"" Ahakan akayi zaman makoki akawatse "" Dan babanta yace bayason wani zama saidai kowa yabita da addua"" aranar kowa yawatse anayiwa habiba Neman gafarar Allah Kowa yazo gaisuwar dole yakoma dason lubabatu acikin ransa ba alfahariba ko mijinta baikaita nuna bakincikiba"" Ahakan akayita lallashin juna"" aranar sukadawo gidansu Hajiya lubabatu harda karamar jinya tayi tarashin kanwarta adole alhaji yabar aikinsa yatsaya jinyarta"" su hajiya kwanansu hudu sukajuya suka koma"" Bayan satii daya darasuwarta yan uwanta sukazo gidan suka kwashe kayansu"" ranarma Ku San kukanda sukayi dasu da lubabatu tankar yafi naranar rasuwarta wata kanwar Innar habiba harcewa tayi da alhaji yanason yarta ai wlh databashi Dan sosai sunason lubabatu kamar yanda takesonsu"" Bayan sungama yan koke kokensu tarakasu sukawuce takoma cikin gida""tasheke dawata mahaukaciyar dariya""" tasoma tafawa lallai kimabashi yarki??? Aikuwa dakin yankarwa yarki ticket din zuwa lahira barganina ahakan bakar kunamaçeni🦂 "nidin damoce Amman nafi maciji hadarii Babu wata wacce ta isah nayi kishi da itah ba ahaifetaba""" idankuwa tsautsayi ya saka wata tashigo gidan nan tabbas tasoma kididdigar ranar mutuwarta tasake shekewa da dariya tawuce saman *WADANSU SHEKARU BAYA* Alhaji adamu yunusa"" wani gawurtaccen maikudine kudikuma bana wasaba"" attajiri wanda yakrtashen kudi yanada mata biyu hajiya binta itace uwargida yayanta uku Usman hafis da kubrah"" sai Amarya hajiya hannatu yayanta biyu duk maza kabeer Ahmad"" Alhaji adamu irin mutanen nan ne wadanda sukeda kudi kamar hauka Amman ba agane hakan ajikinsu kokuma asuturansu domin bayaci kuma baya bawa iyalansa komai nagidan kwab kwab akedashi acewarsa aidukiya tattali take so" idan bahakaba tawargaje😂 Sam yan uwansa abun yanabasu haushi barinma hajiya hannatu dankuwa itah macece maison karya danuna isah Abudayane bayawasa karatun yaransa danyafison kowanne yayi karatu yanemi nakansa dankar zuciyarsa tamace akan na mahaifinsa"" Usman tunda yatashi Sam dukiyar mahaifinsa bata burgeshi tunda yasoma karatu yamaida hankalinsa wajen karatu"" harya kammala degree dinsa fannin kasuwancii"" Alokacin babansu yabasu jari Usman da kabeer dankusan taresuka kammala karatu"" Usman yanada farinjini hakazalika akwaishi dason mutane babu ruwansa dashiga harkar dabata shafeshiba yanada wani aboki akaduna sunansa abdullahi shine kawai abokinsa baban abdullahi dankasuwane shima yakarfafamasu guiwa akan suyi karatunsu bangaren kasuwanci Alokacin da mahaifinsu yabasu kudi yanunawa mahaifiyarsa tasanya masa albarka ranar yakirah Abdul yasanardashi"" Yace gobe zaizo kaduna hakan kuwa akayi mahaifin Abdul yahadashi damanyan yankasuwa yafara sana a Cikin yan shekaru Allah yasakawa dukiyarsa albarka"" alokacinne hajiya binta tafara masa maganar aure"" damakuwa yadade yanason wata ameena wacce take tuyar awara alayin gidansu Abdul Ameena marainiyaçe mahaifiyarta tarasu tuntana yarshekara hudu aduniya"" babu kalar wuyarda bataciba wajen matar ubanta huwaileDuka kuwa dayunwa dasuna kashi datuni sunkashe ameena Mahaifinta yanasonta sosai Amman dagabaya da akaci karfinsa yakoma da itah dababu itah duk daya gashikuma itace kawai yarsa Huwaile tasoma dauramata talle kuma baburuwanta nairah inhar tayi ciwon kai ajikinta Zata debe tashayi mata tsarki da attarugu tawanke mata daruwan zafiii Azaba iri iri babuwaççe ameena batashaba"" tunlokacinda taga tasoma kirgan dangi saitafàra yimata awara tana toyawa alayinsu Dayake unguwar kowayasan mahaifiyàrtà babu Wanda yatabajinta tayi sa insa da makota bakamar huwaile ba harfada takeyi da kartii idansunçi bashinta basu biyaba babu ruwanta dawai itah matar aurece!!! Aisha✍🏼 ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠ Chapter 12 By Gentle Lady💃🏽 Malam garba kuwa dashi da babushi duk daya kobanza yana bala in tsoronta tunda ba banza tabarshiba"" Duk saurayinda yace yanason ameena har gigi yakaishi kofar gidansu huwaile ce zatafito tazageshi ta uwa ta uba"" hakan bazai ishetaba saita samu iyayensa tayi masu Tass kuma tace sujawa dansu kunne kartasake ganinshi kofar gidanta dayawa samari sunason ameena Amman balain huwaile suke gudu"" Tunranarda Usman yaganta yaji takwanta masa arai barinma lokacinda Abdul yasanardashi ainahin tarihinta saiyaji babu matarda yakeso aduniya sama da itah""" Lokacinda mahaifiyarsa tayimasa maganar aure saida yafara neman shawarar abdul akan yasanarda itah"" dariya yasoma yimasa yace zakafara wautar taku ta yayanfari tomenene dankafada mata kokunyarta kakeji"" Dariya yayi yace wacce irin kunya Abdul tunani nayi yarinyar nan bataSanniba kawai dai saninda tamun inazuwa cin awararta lokacinda nake karatu" atunaninka itah zatasoni??? Nifa banaso nacutarda itah Abdul yasake kwashewa da dariya yace kwantarda hankalinka mutumina indai ameena ce wlh bakada damuwa kasan sarai itama kamar akan kayatake agidansu yanda aka azabeta nikam hakan yayima kaga huwaile Batasan da soyayyar kuba ballantana ta fatattakeka Tare suka kwashe da dariya yace fatattakadai abokina aitasan wadanda zatayiwa hakan sudinma rainasu tayi kodayake hakan datayi alhairi ne agareni dayanxu banine zansamu wannan kyakkyawarba"" sosai Usman yarude akan sonta cikinwai ma bata kwalliya Dan huwaile batabari waidan kartasamu samari Ranarda yasanarda mahaifiyarsa tafadawa alhaji adamu yayi murna sosai Amman kafin yanema masa auren saida ya tabbatarda kasuwancinsa dayanda yasamu riba sosai fiye dakudinda yabashi Bawani batalokaci yasanarda limamin unguwarsu dawasu abokansa sukaje kaduna sukanema masa auren ameena awajen mai unguwa Saboda Usman yafadamasu komai akan matarsa""mai unguwa yaji dadi sosai yasa akakirah malam garba" agabansa akayi komai sunbada harda kayan nagani inaso dakuma kudin saka rana ahakan alhaji adamu yace asaka biki kusa kusa kumashi yaron yace basaitayi komaiba shizaimata kayan daki dakomai malam garba kam yayi murna duk dakasan zuciyarsa halbawa yakeyi shikawai yasan fitinarda zaihadu da itah agida"" mai unguwa yace totunda har hakane mezaihana adaurah auren ayanzuma idan ashirye kuke"" hakan bakaramin dadi yayiwa alhaji adamu ba babu bata lokaci yakirgo kudi dubu hamsin amatsayin sadakii Goron saka rana shi akayita mikawa mutane mai unguwa shiyazama waliyin Amarya"" take akadaurah aure jama a suka shaida bayan yan gaishe gaishe"" alhaji adamu da tawagarsa suka kama hanyar kano cikin farinciki Malam garba yanarike da sadakin ameena dagoro yatunkari kofar gidansa gabansa yanafaduwa"" yadade bakin kofar gidan dagabisani yashiga da sallama Ameena tana tsakar gidan tana darzar wankin huwaile da fa Iza " ita kuma uwar ikon tana inuwa zaune tanayiwa fa Iza tsifar kaiii"" fa iza yartace Amman batareda malam tahaifetaba bayan tahaifetane tarabuda mahaifinta saita auri malam Bagidan take zamaba saidai tanazuwa akai akai duk sanda tazokuwa kafin takoma komai ameena takemata duk dakuwa ameena tagirmeta"" malam yakalleta yadauke kansa aransa yace kinkusa hutawa da wahala ameena "" tunkafin yazauna huwaile tamike tanakallonsa yanda yake fara"a Kujerah yaja yazauna yana mai fuskantar huwaile sannan yakwalowa ameenar Kira"" Huwaile tace haba malam yaxaka kirata bayankuma kana ganin wanki takeyi??? Cikin in inna yace ainaga ba wani abubane dannakirata badadewa zatayiba"" tace kaikasan wannan nidanakeso tagama dawuri tafita tuyar awara Cikin malam yahau hautsinawa jin furucinta lallaikuwa akwai aiki jajir"" takatsemasa tunaninsa tahanyar karbe kudin hannunsa tana jujjuyasu tanakallonsa Sunahada ido yaji zawo tamkar zaizubomasa"" tajefomasa tambaya kudin waye wannan??? Yace eyin eyin"" takatsamasa tsawa batambayarka nakeba"" Cikin kaduwa yace dama yarkice kinsan kwanaki kinacemun gashinan tagirma"" Amman"batada mabidi "" kinsan komai lokacine da"" katseshi tayi cikin karaji kamar mai magana da danta tace sai akayime??? Kafito kayimagana kadaina wani yan zagaye zagaye"" Saida yahade wasu yawu yace sadakin ameenà ne"" gakuma goro "" kafinma ya ajegoron tamike tafara liliyo ashar"" tawatsa masa kudin afuskarsa Tace kayi gaggawar daukar sadakin nan kamiyar dasu inda suka fito nibantashi aurar da itah ba"" malam garba yashafo zufar goshinsa yace saidai kiyi hakurii Dan maigama tagama har andaurah auren Wohoho inawuta tasakashi "" jitayi tamkar tarufeshi da Duka"" tace tabdijam wato Dan anunamun iyakata shine akaje waje aka kimtse magana tsofaffun munafukai dama ninadade dasanin duk yan unguwar nan munafukaine Wato ana bakincikin yar tallarda nake doramata saida sukai kutunguilar samomata miji"" tonikuma sainaga wanne shafaffen damaine ya isah yashigo gidan nan yadauketa Tallekuma yanzu akafara hartuwo tuwo zanfarà yimata tanazuwa kasuwa yan bakinçiki saidai su mutu kuma ko anki ko a anso ko anasonmu ko anakinmu dole aganmu akyale Cikin sanyin murya yace kiyi hakuri nikainà badason raina akayi abunba aikin mai unguwane Rufemun baki tsohon munafuki aikaine babban mailaifin kafadamun tareda mai unguwa kukayi cikinta dazaiñuñà maka iko akanta??? Aisha✍🏼 ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠ chapter 13 By Gentle Lady💃🏽 Yanisa bahaka bane kiyi hakuri abun duk baikai na tashin hankaliba"" tayi saurin gwatseshi tace awajen kaba ?? Wato malam dakai za ahada kai acimun mutunci a unguwar nan Saboda banice nahaifi ameena ba?? Amman inda kara aitamkar nidince na haifeta tunda nake auren ubanta kuma bauta wacce hawalane banshaba tunyar nan tana tatsitsiya saiyanzu data girma za anunamun halin karfi bakomai aure ko aje ayi "" inazaune zatadawo tasameni taja hannun fa iza sukashige daki Ameena kuwa tun lokacinda suke maganar tanaduke banda kuka babu abunda takeyi Sam abunda akemata agidan bayadamunta Sama da abunda akeyiwa mahaifinta !"tana tsaka da tunani taji yadafata"" tadago dahanzari takalleshi saita done kanta tacigaba da sharar kwallah"" Yanisa kiyi hakuri ameena ninasan amatsayina na uba bankare maki hakkin kiba dayake akaina"" inajin tsoron tambayar ubangijina agobe kiyama abisa amanarki datake hannuna nakasa riketa Nikaina bansan yazanyiba alal Hakika inason ganin farincikin ki"" yasake jan ajiyar zuciya kiyi hakuri kuma kisa Allah aranki insha Allah zakiga sakamakon hakuri Tagyada kanta nagode Abba inshaa Allah zancigaba da hakuri har lokacinda zanbar duniya Amman Abba auren nan idanhar inna bataso kawai abarshi kwanciyar hankalinka shine nawa banason abunda zai rika sakawa kanasamun sabani da itah"" Ya murmusa karkidamu ameena magana anriga da angama kizama cikin shiri aduk lokacinda mijinki yazo zakibishi"" Allah yabaku zaman lafiya"" inarokonki akan kizauna da mijinki lafiya da yan uwansa "" Tanisa nagode Abba"" kudin yamiko mata"" yace gakudinki"" kanta tasanne kasa alamar kunya"" tace Abba kadauka nabaka Kayi wata lalurar dasu""" Yace haba ameena ina kikataba ganin anyi haka sadakin kinefa?? Tace bakomai wlh Abba""" yace shikenan Amman ninasan mezansiya maki dasu idan bukatar kudi tasameki saiki tambayeni"" tagyadamasa kai kawai"""anan yabarta yashige dakinsa itah kuma tacigaba dawankin datakeyi""" Alhji adamu yakoma gida murna fal ransa"" alokacin Usman yanagida sosai yakagara mahaifinsa yadawo yaji ko ambashi ameena"" saiyasamu labarin harma andaurah aure wani dadine yakamashi tamkar yayi ihu""" dukawa yayi yayi sujjada yanamai godiya ga Allah dayabashi ameena"" Take yakirah Abdul yasanar dashi"" yatayashi murna"" nesa kadan"" dagidansu Abdul Usman yasiye gida Dan madaidaici mai dakuna biyu ajere"" kowanne daki daya dabayi sai falo daya dayake farkon shigowà saikuma bayin tsakar gida""sai kichin komai yasaka acikin gidan daidai gwargwado"" Yakuma tanadi kayan abincinda zasu bukata"" alokacinne yasanarda mahaifin Abdul yasamu mai unguwar yafadamasa Usman yanason abashi matar sa"" domin haryanzu huwaile batadaina doramata talleba"" Mai unguwa yaturah maidakinsa taje gidan tahado mata kayanta"" tatasota gaba ammanfa ansha rigima saida taji alamar za ahadata dayan sanda sannan tabarta"" matar mai unguwa babu laifi"" tagyara ameena daidai karfinta satinta daya agidan mai unguwa akace Usman yazo yadauki matarsa Alokacin ameena tayi Dan kyau tayi yar kibarta daidai gwargwado""" ranar kuwa Usman sukaje tareda Abdul sukadaukota"" Alhamdulillah sunazamansu lafiya babu wata fitina"" saidai huwaile datake zuwa gidan takwashe mata kaya har abinci"" Amman Sam bata taba fadamasaba "" kodakuma abincin yakare dasauri tafadamasa bayacewa komai zaisiyo wani Wataranane huwaile taje gidan harda mai baro Wanda za alodo kaya saboda tamiyardasu hajarta"" dankuwa har suturah takedauka"" barta ameena harta Usman dauka take"" aranar tayi rashin sa a kubrah kanwar Usman tanagidan""" Dashigarta"" ameena tanazaune kotakanta batayiba kallon banza"" kawai tawa tsamata tawuce kuryar"" dakin"" Tasoma jido kaya"" tana ajiyewa bakin kofa"" daidai fitowar kubrah tace La Anty wanki zakiyine shine kokimun magana intaso intayaki bayankinsan kwance kawai n"" batakarasa rufe bakintaba saiga huwaile dazannuwan gado"" Sabbine hull maman Usman tasiyomata su jiya kubrah takawomata""" aikuwa kubrah damamaki takalleta tace wannan kuma wacce mahaukaciyarce????? Sai alokacin huwaile tadago kai afusace tace uwarkice mahaukaciya yar iskar yarinyà"" aikuwa batama rufebakintaba kubrah tadauketa damari jikake tasss Batagama mamakiba"" tasake dauketa dawani"" Marin tareda nunata dayatsa karki kuskurah wlh mahaifiyàtà bakalar zagi bace ki kiyaye harshenki Sannan kisan kalar furucinda zakiyi agidan nan"" daganinki nasanke kowacece"" taduka tadauki kayan tawuce tagefenta hartana tureta sainagani idan ubankine yakesiyo kayan Huwaile tanatsaye rike dakumàtu baki bude takasa cewa kala"" har kubrah tagama miyarda kayan"" itakuma ameena tamkar gunki takoma sai rarraba ido takeyi""" Tadawo gabanta tareda kyasta yatsunta biyu"" daidai saitin fuskarta"" tace oya mekike jirah kama hanya kibar gidan nan tunkafin inrasa natsuwàta wlh inlakadamaki shegen dukanda yausaikin kwana agadon asiviti"" Hannunta dafe dakunci tawuce sumui sumui"" kubrah tadakamatà Tsawa Keee!!! saida tazaburah harsaida guntun zawo yazubo awandonta""" Kubrah tace sauran idan bananan kisake wanko wannan jemammar kafartaki maikamada kashin shanuu kidawo gidan nan hmm wannan gargadine nakemaki Dan muddin nasamu labari hargidanki zansameki inlakadi banzaa tsohuwar banza wacce batasan Allah ba ke kokunya bakijiba kisamu marainiyà kina zalunta" kebaki kawomataba kidauki nata"" Bàrima nahadaki dahukumà suje hargidàñki sudibomatà kayanta"" dannasan bawannan nezuwanki nafarkobà!! Aisha✍🏼 ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠ chapter 14 By Gentle Lady💃🏽 Cikin fushi kubrah tajuya dakin domin dauko waya"" aidasauri huwaile tafita ko takalmanta batajirah tadaukaba yau Allah yahadata da hatsabibiyar yarinya kuma take taji tsoronta harcikin ranta Tana rayawa aranta lallai kubrah ba itah kadai takeba kokuma tanada tabin hankali"" dasauri takoma gida tareda danbaro tasoma jido kayanda suke gidan wadanda bata salwan tarba tadorawa danbaro tace yakawo gidan dataje dashi yanzu yadawo tabashi kudinsa""" Tashige dakinta takulle"" jikinta sai kyarma yakeyi"" bayan fitarta gidan kubrah tafito daki tana kallon ameena tasheke da dariya tace Anty yanaga duk kintsurene???? Tanisa badoleba bakisan halin inna huwaile ba wlh masifaffiyace babana ma tsoronta yakeyi nayi mamakin daharkika mareta batace komaiba"" Kubrah tasake shekewa da dariya tace aiyauta gamuda daidai itah kudinne kuke kyaleta na tabbata yau saitakwana gudawa"" sallama sukaji akofar gidan"" Ameena tace shikenan wlh tadaukoman yan sanda"" kubra tsaki tayi tace kwantarda hankalinki Anty indai inagidan nan wlh ba dansanda zatadaukoba tadauko alkwali ni daidai nakedashi danni walkice daidai kugun uban kowa"" tayi maganar tana Jan mayafii tafitaa fuuu Tana bude kofa taga maibaro dakaya"" akatunan da Usman yayiwa ameena duka tadibe"" kubrah cike da mamaki haka tayita daukar kayan tanakaiwa cikin gidan saida takwashe duka sannan tacewa danbaron kafadamata nace ta saurari sammacii akotu sainasa andaureta"" Takoma cikin gidan"" tasamu ameena tanabuda kayan""" tace waiyanzu Anty fisabilillah duk kayanki matar nan takwashe kallifa harda abinci kuma kizubamata ido???. Matar nanfa ba itah tahaifekiba??? Tanisa toyazanyi kubrah ni fitinane banaso kawai Dan azauna lafiya itah abun duniya yadama "" nakyaleta aiba anan za atabbata ba"" kubrah tace hakane Amman hakurinki yayi yawa Anty aiwannan wlh tacutardake sosai tunfarko danasani aida sainasakata tsallen kwado wlh agidan nan""tare suka kwashe da dariya"" Ameena tace koyanzu aitatsure nibanyi tsammanin tanada tsoroba wlh"" kubra tamiyar mata"" da kayanta duka dakinta Danbaro yana komawa yashaidawa huwaile sakon kubrah saiga huwaile tabarke dazawo"" yinin ranar daki tawuni kulle dataji motsi anshigo gidan tashige karkashin gado"" saida aka kwashe sati biyu sannan huwaile tasoma fita"" Amman batasake gigin zuwa gidan ameena ba"" Ko ameena tazogidan nan babu ruwanta da itah"" tsayin shekaru uku da aurensu Amman batasamu cikiba"" kokadan Usman baidamuba alokacin Abdul yayi aure matarsa"" Hauwa"u Watan bikin Abdul ameena tasamu ciki"" alokacin kuma Allah yabudewa Usman kofofin arziki kasuwancinsa yafara habaka saigashi ansoma damawa dashi cikin masu kudin garin Tuni yasiye babban fili kusa da gidansa""" akasoma gini"" hawa hudune akayi gini Wanda yakeshine"" bayan cikinta yashiga wata Tara"" tahaifi danta kyakkyawa kinkowa Wanda yarasa sati yana zagayowa akaradamasa suna khaleed Sosai Usman yakeson yaronsa"" suna kuladashi bama kamar kubrah"" kaleed yanada shekara daya mahaifin Usman alhaji adamu yarasu bayan doguwar jinya dayayi sosai mutuwarsa tagirgiza su Usman Sunagidan har akai sadakar uku sannan sukadawo gidà"" su hajiya sunagama takaba hajiya hannatu tace araba gado abata na yayanta damakuwa tanajin haushin Usman saboda kudinda yayi lokacinda akabasu kudi suja jari da danta kabeer duk ya halakarda nashi wajen Neman mata"" dakuma shaye shaye"" Babu wani bata lokaci akaraba akabawa kowa hakkinsa"" take ta tattara yayanta da dukiyarta suka koma bauchi damacenne tushenta"" mahaifiyar Usman tahademasa dukiyartà data kannensa yafarayimasu kasuwanci dasu shikuma nashi yahade danasa""" Cikin shekaru uku Alhaji Usman yazama dai dagacikin masu kudin Nigeria"" idan za akirga masu kudi a Nigeria inhar baizo nadayaba babu shakka zaizo nabiyu"" tuni angama ginin gidansa yatare tareda matarsa dakuma dansu kaleed Sam alhaji Usman baida sha awar yin aure"" saboda ameena tanayin bakin kokarinta wajen biyamasa bukatarsa batagajiya da yawan bukatarsa kuma azamansu basutaba yin fadaba kowannensu hakurii gareshi""" Kaleed yanada shekara biyar kubrah tayi aure"" mijinta yana karatu maleshia"" aurensu dasatiii daya sukadaga cikin jirgi zuwa maleshia Dajine mai matukar duhuwar gaske"" bakajin motsin komai awajen hartakukàn tsuntsaye""" zaune take saman wata shimfida"" tana fuskantar kogon"" wata karaaa najiii wacce tayi sanadin zaburata hardawacce takezaune Bishiyar kukarda takecikin kogon tasoma amsa kuwwwa wacce tasakani rufe kunnuwaña"" wata wutace tayi tartso tareda walkiya haske yafaltsu sama saiga bishiyar tarabe gida biyu""" Wacce takezauñe awajen tasaki murmushi""" lubabatu kenan wacce akafisani da lubcy!! Aisha✍🏼 ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠ chapter 15 By Gentle Lady💃🏽 Lubcy yar kasar bauchi ce Amman iyayenta duka aikin gwamnati sukeyi zamane yadawo dasu"" legos Su biyarne awajen iyayenta hudu maza itah ce kawai mace"" iyayenta rikakkun yan boko ne shiyasa sukeson yayansu suyi zurfi wajen karatun boko baburuwansu dawai susaka yayansu islamiyya"". Sudai burinsu yayansu suyi karatu inhar anaganin karshen biro da takarda babu shakka yaransu zasugani saikuma akayi rashin sa a lubcy dakikiya ce yanda kukasan dusa haka kanta yake bata iyah rike komai harta sunanta bata iyah rubutashi daidai Tunsanda take primary batada wani kokari duk akayi jarabawa ita take kulle ajinsu"" babu yanda babanta baiyiba komai takeso zaisiyamata Amman abanza dayake babanta maikudine sai akarika badakudi anazauna mata jarabawa hartasamu ta kammala primary da secondary sai yaturata America Acen tahadu da wasu mugayen kawaye sadiya"" da rabi atu sajida da anisa"" dukkanninsu hausawane"" tare suke tsula tsiyarsu saboda duka basada kokari kodasunje ajima babu abunda suke iyah ganewa Zaune take cikin skull dinsu wata bayeraba tana kusa da itah tanawaya department dinsu daya da itah kusan duk akai jarabawa itah take lashewa""" Aranta tace wannan dai babu alamar kokari gareta kodayake baridai nasamu nakullah abota da itah konasamu inji metakesha takeyin wannan kokarin Tashi tayi tataka zuwa inda take tace hye"" sannunkida hutawa"" tadago takalleta tace yewwa sennude"" Lubcy tace zan iyah zama"" anan??? Tasaki fara a bademuwa zauna"" lubcy tazauna tabata hannu sunana lubabatu Amman zaki iyah kirana da lubcy .tajinjina kai tace am heelin"" by name Lubcy tamurmusa tace suna maidadi"" heelin tawaro ido tace dagaske kinayi?? Lubcy tagyada kai heelin tace tnx dea Duk da lubcy batagane Hausar heelin Amman haka ta manne mata harsuka sabu"" ansoma shirye shiryen fara jarabawa suna zaune dakin heelin lubcy tanata duba littafi dukda batagane komai dankar heelin tacewani Abu saitaga itah heelin din Sam bata karatu saima danne danne takeyi awaya"" Takirah sunanta tadago takalleta tace yadai friend?? Lubcy tanisa tace waike banganki kina karatuba kinsanfa ankusa fara jarabawa "" heelin tabushe da dariya tace ai wahala saiku nibana karatu ai""" Tace kamarya??? Toyakuma akeyi kina cinye jarabawa??? "" tayi tambayar tana kallonta murmushi tayi sannan tatashi zaune tana kallonta taciro wani biro tanuna mata tace kinga wannan?? Lubabatu tagyada kai"" tacigaba dazeran nadorashi akan takarda nawa dekansa zairubutamun amsa"" lubabatu tazaburah tace biron??? Heelin tamurmusa tace shifa"" wannan nasamoshine awajen wani boka" sunansa *HATSABIBIN BOKA* duk wani bukata nawa wajenshi nakezuwa take zaibiyamun dabukata Nitunda nake baburuwana de karatu" kuma danagama wajensa zanje yasamamun aiki mechau""" Tuni lubcy tadawo kusa da heelin tace Dan Allah Kawata nima kikaini wajensa yabani"" heelin tace anya zaki iyah kawayenki ma sunyimun magana Amman nace bazasu iyaba saboda kinga addinina de naku badayaba"" bazaku iyah bin dokokin siba Murya narawa tace wlh komenene zamu iyah indai zaibiyamana bukatarmu heelin tace inde wannan ne atake kuwa"" saiki fadawa kawayenki kushirya sainakaiku Lubcy tayi ihun murna tarungume heelin"" aranar tasanarda su anisa ranar weekend sukashirya sai taraba acenne garinsu heelin Amman basuje gidansu heelin ba suka samu hotel sukahuta anan"" anasoma kiran magrib sukafita zuwa dajinda yake Cikin kauyen taraba yake"" ka idar zuwa wajensa"" inrana tayi tsaka harzuwa dare"" tundasukashiga jejin jikinsu lubcy yasoma rawa fitiluni gasunan cikin jejin suna reto kuma ba daure sukeba basu sama basu kasa""" Gabadaya ajikin heelin suka labe bakin wani katon iccen kuka suka iso"" kasansa anzagayeshi da karaa saman karan lullube sukeda fatuu Na namun jeji"" babu alamar kofa awajen heelince tasoma wadansu suruttai na gwalamniya"" tana kiran sunansa *hatsabibin boka* take dajin ya amsa kuwa"" takesu lubcy sukasaki fitsariii ganin wutaa Yakama bakin wajen balbal kaitsaye heelin taja hannun lubcy tatuñkàri kofar""" Aikuwa lubcy tadaddage zatafasa ihu saidaime jitayi muryanta yadisashe"" heelin tasake jawo hannunta tana tirjewa sukashigà tacikin wutar"" saigasu cikin daki maigirman gaske"" su anisa sunawaje jikinsu na kyarma kowacce tacika wandonta da fitsari Aisha✍🏼 ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠ chapter 16 By Gentle Lady💃🏽 Jira suke kawai ace kat su yanki nakare""wata tsawa aka dakamasu wacce tayi sanadin faduwarsu su uku duka asome"" Heelin da lubcy suna samun kansa cikin babban dakin"" saiga wata shimfida kamar tabarmar kaba"" tataso zuwa indasuke tashimfida kanta"" batareda wani tsoroba heelin taja hannun lubcy zuwa saman shimfidar cikin tsoro tazauna gefe zaunawarsu yayi daidai dazubesu aneesa saman shinfidar take kuma suka farfado tamkar wadanda aka watsawa ruwa"" Nanfa suka soma kallon kallon aneesa tasoma kuka"" Dan tarigada ta sadakar mutuwarsuce tazo Dukansu arikice suke inka debe heelin wacce ko ajikinta da alamu Sam batadamu dakomaiba dantasaba "" wata rikitacciyar tsawa akasaki"" tayi tartso"" bakin bishiyar yasoma cidawutaa tareda wani kugiii Yan hanjinsu lubcy har motsi sukeyi""" tsawar tacigaba da hauhawa tareda darewar katuwar bishiyar kukar zuwa gida biyu"" wata kujerace tafito zuwa daidai kusa dasu lubcy tatsaya chak""" Kafin kiftawar ido wata guguwace mai karfii tataso wacce tasaka gabadaya wajen yahautsine baka iyah ganin komai wannan karon ba su lubcy ba hatta heelin saida ta kare fuskarta datafin hannuwanta""" Su lubcy kuwa gabadaya suka kankame junansu jikinsu yana kyarma tamkar mazari"""tsayin mintuna biyar komai nawajen yakoma kamar yanda yake kurar wajen talafa saiga *hatsabibin boka* ya bayyana asaman kujerar"" Heelin ce tafara zungurarsu lubcy dukansu suka"" bude idonsu"" wani gabjejen mutum sukayi arba dashi Wanda basutaba ganin koda maikamadashi ba acikin duniya wannan zaifikyau akirashi da dodo Kaiyamafi dodo muni saboda katone majiyi karfii yanada damatsa manya manya tamkar irin namasu danbe""" kowanne damtse nashi daure yake dalayu nafata dakuma wani kambum karfee Kafarsama haka""" baya sanye dariga"" cikinsa dame yake Amman kanaganin gurayenda yatara ajikinsa""" yanada tsayi sosai dantsayinsa zaiyi kamu ashirin"" kirarsa tamkar Wanda yayi alaka da samudawa"" Bakine wuluk tamkar bakin kwalta bakaganin komai afuskarsa sai jajayen idanuwansa"" kowanne mutum tsakiyar idonsa bakine ammanshi kuma zaibarda take zakiyar idonsa"" farace tass saikuma ja azagaye da itah""" Idan yadaga ido gabadaya"" farin facewa yakeyi "" saidai ja yamamaye gurbin ido"" sumar kansa tanada yawa Wanda yawanta yasa tazubo har akan faffadan kirjinsa tayiwa mummunar fuskarsa inuwa wannan mutum dazaifito waje babu shakka dayawa mutane zasurasa rayuwarsu sanadin yin Arba da mummunar fuskarsa mai kamada ta dodanni"" Tsayawar guyuwar keda wuya yakece dawata mahaukaciyar dariya wacce tasaka dajin gabadaya ya amsa kuwa"" yadauki tsayin mintuna biyar yana wannan dariyar dagabisani yamurtuke fuska tamkar Wanda baitaba dariyaba"" heelin tabuda baki tasoma jero masa kirari"" Saikai takadiri kuma gagare kigudu sagudu sa abokan gaba sugudu""" Turmin karfe kake shakwaramniya""" Saikai *hatsabibin boka* sugaban duk wani tantirin ajani"" komai Tsagerancin aljani idan yazo gabanka dole yaduka nasaramaka uban maza uban hatsabibai maidakawa maza gumbaa""" take yasake kecewa dawata mahaukaciyar dariyaaa Heelen tasake buda baki daniyar magana yadaga mata hannu Yace kafin kice wani Abu inaso insan kokin sanardasu dukokinmu dakuma sharadin mu??? Cikin saurii tace nafadamasu yasarkin bokayen duniyaa Yagyada kansaa duk dahaka zansake sanardasu dangudun kuskure dakuma fadawa hafushinmu""" kusanii akwai sharadiii guda biyar wadanda zanfadamaku Inhar kuka kiyaye kuntsira sharadi nafarko"" ma abota sallah basa shigowa fadataa""" duk ranarda zakuzo inda nake karwacce takuskurah tadorah goshinta akasa"" Sharadi nabiyu"" karwacce takuskurah tabada sadaka!! Domin yanadaya dagacikin abunda zaibata aikina""" Doka ta uku muddin kika fara aikidani babuke basake zuwa wajen wani bokan "" yinhakan kuwaa zaijanyomaki masifa da bala.i dagake harbokan nakii Sharadi nahudu duk abunda akace kikawo karkitsaya musu ko gardamà idankuwa kikatsaya watamagana take bakaken aljanu zasu zuke jininki Doka tabiyar wajibine idan akabaki Abu dole ki aikata idankuma kinki to zaijuye zuwa kankiii""" sannan kuma duk abunda kukagani anan karkutaba idankun kiyaye kuzauna lafiyaa Tunsa inda yasoma wannan jawabin jikinsu sadiya yasoma kyarma dama yalafiyar kurah kowaccensu tayi danasanin zuwa wajen yanagama rattafo sharadansa saisuka fara kallon kallo atsakaninsu gabadaya idonsu yaraina fata"" Lubcy tanason yin magana babu halii "" saida yabata izinin magana cikin sauri tace"" dama dama munasone mudanyi shawara Batagama rufe bakintabà yadakamata wata razanan nar tsawaa wacce tasaka lubcy tayi danasanin maganar Hatta dakin saida ya amsa kuwaar yace bakuda wannan damar kusani kafin azonan akeyin shawaraa basai anzobaa danhàka Ku kiyaye!!! Aisha✍🏼 ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠ Chapter 17 By Gentle Lady💃🏽 Cikin kyarma lubcy ta gyada kantaa heelin ce tace tuba suke"" uban hatsabibai"" sunji kuma sunyarda da sharuddanka idan muka fitaa zamu turoda kayan aikiii yajinjina kai" saiki sanardasu zasuga abunda sukeso""" tadan dukarda kai tace godiya muke""" tasake dukawa tace munbarku lafiyaa"" sannan tamike aitana tashi su aneesa sukai zumbur suka Mike dama Kuwa kamar akan kayasuke""" Kamar yanda sukashigo wajen yarufe kansa babu alamar"" kofa"" suna fuskantar wajen"" heelin tasake kiran sunansa saigashi wajen yasake kamawa dawutaa suka ratsa tacikin wutar saigasu waje"" Gabadaya dajin yayi tsit saiwani gurnani sukeji kamar na kuraye da zakuna suna nane da heelin harsuka kai karshen"" dajin"" tace duka surufe idonsu Rufe idonsu sukayi kafin mintuna talatin sukaji tace kubude suna budewa sukagansu cikin masaukinsu"" aneesa cikin tsoro tabuga uban ihuuu tashige cikin zanen gado""" Heelin takwashe da dariya tace Amman kumanyan matsoratane nibantaba ganin masu tsoro kamar kuba"" jiyanda kuka tsure kamar kusaki zawo awando Lubcy tace heelin ai ba kamabane"" ni bana raba dayan biyu wlh fitsarina sau biyar awando idan ancema harda zawo bana musawa sainashiga toilet in tabbatar,""" Sadiya datake sharce zufa tace wlh nima fitsarina shida awando kai nadaukafa mutuwa zanyi niko amafarki bantaba tunanin zantaba ganina a irin wannan wajenba""" Wannan anyakuwa mutum ne??? Idankuwa har mutum ne anyi mumm bata karasa rufe bakintaba heelin ta dademata baki tace wlh karkisake duk abunda kikeyi tamkar agaban *hatsabobin boka* kike!!jin wannan furucin yasaka sadiyaa saurin hadiye wasu miyagun yawu masu dacin gaske idanuwanta suka firfito kulu kulu tamkar wacce taiwa sarki karya"" tace nashiga uku kardai yakasheni tayi maganar tana dafe kirjinta""" Heelin tace bazai kashekiba saidai zaisa akaiki kurkukunsa Wanda yake ganawa bokaye azaba dakuma wadanda suka bijirewa umurninsa cikinsu kuwa harda aljanu"" zamanki acikin kurkukun saikin gwammacewa mutuwarki akan haka domin zakisha azaba iri iri wacce bakitaba tunanin irintaba""" Zaiyafemaki sabodake sabuwar zuwace bakisan komaiba Amman daga wannan ki kiyaye kisan abunda bakinki zairika furtawa""!! Duk yanda kike tunaninsa yawuce saninki"" nikaina awajen mahaifiyata nasamu damar ganinsa"" babuwani boka dazaishige gabansa inhar zaku kiyaye sharudansa har abada bazaku nemi Abu kurasaba kudenajin sorofa"" anisa"" nasan kinfisu jin soro"" dukanku kuyanke shawara gobe zamuje musiye kayan aiki"" saimu aikamasu Aneesa wacce haryanzu batafito acikin zanenda tarufe kantaba tace badai wajen zamusake komawaba??? Heelin tayi murmushi tace ah ah gobedai zakuga yanda zamuyi yanxu kutashi mushi abunshi"" saimu kwanta nagajii woo Tayi maganar tana mikewa tayi hamma"" sannan tawuce "" dukansu ido zuru zuru suma sukamike lubcy kam dayake tanada dakakkar zuciya hartadainajin tsoro Sukai wanka suka shirya"" bayan sunci abinci kowaccensu tasamu wuri takwanta dukansu sukayi lamo tamkar masu barci Amman azahirin gaskiya ba barcin sukeyiba zuciyoyinsu sunyi nisa wajen tunanin inda tsautsayi yajefasu kokuma ince sukajefa Kansu Inkadebe heelin wacce takeyin chat hankalinta kwance"" sai dariya takeyi da alama tanayin fira mai dadi wacce take sakata nishadi"" Intakaice maku labari darendai kam basu samu barciba kowaccensu saiganin abunda sukajeyi take tamkar anayimata video nashi heelin kuwa tashaki barcinta Indasuma saida asuba barcin yadaukesu"" basu suka farkaba sai shadaya narana"" bayan sunkimtsa"" sunci abinci suka shirya heelin tace suje suyi"" abundayake gabansu"" suyiharamar komawa"skull"taresuka fita zuwa kasuwa dama sunzo dakudii heelin cemaidubawa""" duk inda sukaga bunsuru baki Wanda bashida sulkin farii dakuma maifari akai"" uku kawai sukasamu sukai ciniki"sukabiya"" heelin tariko su sukafito kasuwan""koda sukafito basugakomai hannun heelin ba""" Lubcy ce tace ke heelin ina suke??? Tayi maganar tareda soma waigen bayansu takesuma su aneesa sukasoma dube2 kowai tabarsu abaya"" Heelin dariya tasoma yimasu tace waiku kundauka nasakesune??? Ai hadiman aljanunsa sundaukesu yanzun haka akwai sauran su sunajirah mukarasa siyen sudauka tace yanzu wajen da akesiyarda kaji zamuje" Sudaikam binta kawai sukeda kallo haka sukaje sukasiye kaza maiwake Wake sai jajayen zakaru tareda farar kazaa"" Kamar yanda wadancen sukabace hakama kajin"" daganan sukadawo gidansu sukayi haramar komawa skull Ranar sukadawo america kowaccensu tasamu Biro acikin kayanta"" zokuga murna tunkafin suzana jarabawar"" hankalinsu kwance basayin wani karatun har akasoma jarabawa Dazaran sun kalli Question sukadorah biron takezasuga sunata rubuta amsa sukansu basusan tayama amsar take fitowaba Bayan ankare jarabawa dukansu sukalashe"" wannan shine ainahin yakininsu akan wannan *hatsabibin bokan*tundaga lokacin inhar bukatar waninsu tatashi cenyake zuwa hartakaima suna iyah zuwa mutum daya badole saida Dan uwansaba Harsuka kammala makarantar sunkomagida kowacce dasakamako maikyau ranar mahaifin lubcy saboda jindadi yayimata kyautar dankareriyar mota tareda babbar waya"" Tun lokacin batasake waiwayar *hatsabibin boka*ba saiyau kome ketafe Da itah oho!! Aisha✍🏼 ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠ chapter 18 By Gentle Lady💃🏽 Lubcy tasake sakin murmushi ganin wata katuwar darduma irinta sarakai tafito acikin katon kogon kukar tayiwa kanta mazauni akasa"" nantake iska mai karfiii tatashi tamkar ana hada hadari tsawa tareda hargowa sukacika dakin kogon"" saiga *hatsabibin boka* ya bayyana asaman dardumar nantake komai dayake wajen yatsaya chak iskar sannu ahankali tanatse"" Lubcy tadago cikin girmamawa tafara mika gaisuwa tareda somayimasa kirari"" saikai hatsabibi uban hatsabibai"" abuga adaka sai kalwa""saikai namijin gaske uban duka bokayen duniya"" Shugaban shaidanu uban hatsabibai kai kanka tsoron kanka kakeyi"" anbuga dakai anbarka"" kowa yatabaka yanemawa kansa bala i Saikai uban dawa uban kangararru"" takawarka lafiya kaci zamaninka kaci nadangi bakada tsoro bakasan tsoroba " komai gaba kabashi ba nayaba"" Sosai *hatsabibin boka* yake jin dadin kirarin nan tace gaisuwa nake shugaban bokaye kaiyajinjina"" TaCe ayimun afuwa tsawon lokaci bandawo nanba kasancewar daga garinmu zuwa nan akwai tafiya yanzun mawata bukatace dani maigirma"" ina Hannu yadaga mata yace bakomai munsan komai agamedake domin munatare dake"" dangane dabukatarki kuwa tuni nasanda itah wanne irin miji kikeso??? Take lubcy tawashe hakorah jin *hatsabibin boka* yasan da bukatarta"" tace inason mijine na nunawa sa a kyakkyawa maikudi kuma maitashin kuruciya tunbayan gama karatuna zuwa yanzu duk wadanda sukezuwa wajena basuyimun ba Indai kudi sunadakudi saidai suntsufa sannankuma basuda kyanda yadace ace kamata nazama mallakinsu"" wannan dalilin yasaka nazo wajenka domin nasan Kaine zakasharemun hawayena kabani mijinda yatara dukkan abunda nalissafo ayanzu Tanarufe bakinta *hatsabibin boka* yakece da dariya yace kinkawo kuka inda za asharemaki hawayenki yadaga hannunsa sama saigawani madubi maigirma ya bayyana ahannunsa"" Take yashafa gilashin yanawadansu suruttai""" saiga hotunan mutane sun bayyana acikin gilashin su goma sha biyar"" Yanuna mata yace kiduba saiki zabi daya dagacikinsu"" jikin lubcy har rawayake sai kallonsu takeyi tarasa wanne zata zaba" saboda kowanne yanada nashi kyan babu makusa""" Idonta yatsaya akan wani matashin saurayi Wanda yafisu kuruciya daganinsa ko aure dakyar idan yayi"" takafeshi da ido batako kyaftawa""" Ganin hakan yasaka madubin yajuya wajen *hatsabibin boka* take yakece dawata mahaukaciyar dariya yace wannan shikika zabà??? Cikin sauriii tace ah Yagyada kai sannan yaja layi daidai saitin photon"" zuwa yan mintuna kadan yadago yakalleta yace wannan saurayin sunansa Usman sunan mahaifinsa adamu mahaifiyarsa binta yanada kanne biyu wadanda suke daki daya Hafiz da kubra Akwai yan uwansa kabeer da ahmad 'abokinsa daya Abdul"" yanada mata sunanta ameena sunada yarodaya kaleed yanzun shekarar yaron biyar aurensu shekara Tara"" asalinsu yan kano ne Amman yanazaune akaduna anan yake kasuwancinsa yanafità kashashe""" yanzun haka yana maleshia"" kwanansa biyu acen gobe zaikoma gida"" mahaifinsa yamutu yabarmasu dukiya maitarin yawa wacce basusan adadintabà Dukiyardà hatta tattabakunnen su bazaitaba talauciba"" yakai karshen maganar yana kallonta Tayi shiru Sam batayi tunanin yanada aureba"" tadago murya cikin damuwa tace yanzu yaza ayi Sam wlh banasoñ kishiya banyi tunanin yanada aureba"" Yace kwantardà hàñkàlinki komai awajenmu maisauki ne ammanfà kisañi muddin tàñaràye bazaitaba aurenkiba Lubcy tadafe kirjinta tace nashiga uku to akasheta kawaiii Yasake kecewa dawata mahaukaciyar dariya yace wannan daidaine"" kisa aranki yazama mijinki"" tace toyanzu taya zanganshi alhalin yana kaduna ina legos ???? Yasake kwashewa da dariya yace ko birnin sin yake kina sokoto kisani dazaran munturashi dole yaje inda kike"" abudaya zakikoma gida kafin mugama aikinmu akan matarsa daganan zamu sanardake inda zakuhadu Amman akwai sharadinda zangindayamaki karki kuskurah tsautsayi yakaiki fadar sunansa inhar bashine yafadamakiba hakazalika danginsa kinuna tamkar bakisan komai gamedashiba sai idanshine yasanardake Sannan aranar kiyi shigar mutuncii"" komai dazaifaru tsarinane saiki kalli abunda zaifaru"" Yasake daga hannunsa sama saigawañi madubi karami ya bayyana ahannunsa"" yamikamatà Bayan takarba yace kasancewar tafiya mainisaçe tsakaninmu Na mallàkà miki dai daga cikin madubin taskar *hatsabibin boka* aljanin da yakegadiñ wannañ madubin sunansa dukursusu""" kisani wannan aljanin hatsabibin aljanine kuma azzalumi inharkikai wasa da madubin nan dakansa zai halakaki babuwanda zaitaba tunaki aduniya Kirikeshi tamkàr rayuwarki karkibari wani yaga inda kike ajeshi"" bacewarsà daidai yakeda tonuwar asirinki Dazarañ kinada wata bukata tokishàfi fuskar madubin kikirah sunana sau uku zanbayyana acikinsa sàiki sanardani bukatarki Aisha✍🏼 ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠ chapter 19 By Gentle Lady💃🏽 Duk maganarda zamuyi saimuyita atake tamkar kina nandin wannan saukine agareki bake kadaiba akalla akwai su wajen mutane sama da milion daya wadanda basa iyah zuwa nan saidai muyi magana cikinsu akwai yan kasuwa dakuma manyan attajirai dakuma shuwaga banni"" danhaka saiki kula Kuma ki kiyaye idan kinfita saiki kirah aljaninda ke kulada wannan madubin domin yakaiki gida"" dankiyaye lafiyar madubin Yana gama fadar hakan wata guguwa mai karfiii tazo"" take wajen yakaure da iska"" guguwar tayi sama saida tagama shawagi kasar wajeñ tadare gida biyu tashige karkashin kasa bat tabace komai nawajen yakoma daidai Lunby mikewa tayi madubin yana hannunta takaraso bakin kofar bayan takirah sunan *hatsabibin boka* kofar takama dawuta takutsa tacikin wutar tafito""" Tsaye tayi tana tunanin sunanda yafadamata na aljaninda ke gadin madubin Sam tamanta"" lallai dole taje hotel takwana washe gari takoma gida"" jakar hannunta tazuge daniyar saka Dan karamin madubin wata tsawa aka dakamata wacce takusan sakawa lubcy tasakii madubin Cikin daga murya akace"" wannan shine kulawar dazaki bashiii kisani duk kika kuskure abudaya rayuwarki zatashiga hadariiii yanda maganar taketa amsa kuwwa acikin jejen tuni lubcy tasaki fitsari duk darashin tsoronta Dan abuguda takijini aduniya taji anyimata maganar mutuwa kokuma ace zatarasa ranta Natsuwarta batagama dawowaba wata iska maikurah tataso wajen tayi sama""" wacce dazata daga kanta bazataga karshen guguwarba""" tuni lubcy ta kankame jikinta kafin tayi wani motsi kawaitaji an sunkuceta anyi sama"" take yalulaya da itah cikin gajimare Al amarinda yasa lubcy tasome danta sadakar kasheta zaiyi"" batakara sanin meke faruwaba saidai ta far fado taganta kwance akan gadonta"" Jakarta tana gefenta . gakuma madubin ajiye akusa da itah dasauri tamike tasoma yandube dube babushakka dakinta take"" idanuwanta suka sauka akan agogon dakin Wanda yabuga karfe hudu na dare"""tashafo fuskarta yaukam tasake tsorata da lamarin wannan bokan dolema akirashi *hatsabibin boka* domin yaci sunansa"" mikewa tayi daga kan dagon"" tasoma neman inda yadace taboye wannan madubin""" wani karamin akwati tadauko tasakashi aciki tarufe takaishi cikin lokar karamin gado"" take akwatin yafito yadawo kasa"" Tayi shiru aranta tace watakil mazaunin baiyiba tayita tunanin inakuma zatasaka "" karshen lokar kayanta takasa tabude tasakashi Tana ajeshii"" taga yazauna daram tasaki murmushi"" sannan tarufe lokar tacire kayanta tawatsa ruwa takoma takwanta""" Batasake farkawaba sai washe garii""" mamanta Sam batasan lokacindà tadawoba tasan kodasuka kwanta batagidan"" Amman sambata damu data tambayeta inda tajeba aganinta ai itah ba yarinya bace daza atuke da tambaya danyanzu tarigada ta mallaki hankalin kanta Wautarda dayawa mafiyawan iyaye sukeyi ayanzu"" waisunaganin yayansu sungirma sun mallaki hankalinsu bazasutaba kaikansu indasukasañ zasu cutuba Shinmezai hana idan yayanku zasufita kutambayesu inazasuje???" Idankuma sundawo kutambayesu indasukaje harsukai dare Sautari yammata da samari sukan lalaceñe"" asanadin rashin kulawar iyaye mafiyawan lalacewar tarbiyar yayanmu"" munada hannu aciki iyaye sunataka muhimmiyar rawa wajen lalacewar yayansu Kowa yasan akwai kaddara Amman Kuma akwai sakaci"" Allah yashirya mana zuri armu ameeen Lubcy kam hankalinta kwàñce tacigaba da harkokinta *KADUNA* Ameena ce cikin kitchen din gidanta tareda masu aiki tanahadawa Usman abinci domin sunyi waya lokaciñda yake shirin shiga jirgi Tana saran kara sowàrsà biyar na yamma"" gefenta kaleed ne tsaye yana kallonta duk inda tayi yanabiye da itah kamar jela""" Harsuka kammala hadamasà hadadden girki Wanda tasan yanaso gabaya tajeresu akan dinner"" anan tazaunarda kaleed tàzubamasà soyayyen nama tace yazauna tana zuwa . Ta umurci mai aiki tagyara wajen"" akashare akagoge tàjona turaren wutaa"" tuni gidan yarude da kamshi ganin harhudu tagota dasauri tahaye sama dantayi wankaa Tana turah kofar dakintà tàyi tozalii dawasu manya manyañ beraye kowanne daya yakai girman Dan akuya sunada kunba zaro zaro hakorañsu kowanñe yafitodaga bakiñsa zuwa saman labbansa idanuwansu manyane tamkàr kwayayin fitila saidaisu jajir suke kamàr gautaa ihu tafasa dakarfi tarufe idonta ganinsuna tunkarota tàkejikinta yasoma kyarmà Aisha✍🏼 ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠ chapter 20 By Gentle Lady💃🏽 Jikinta sairawa yakeyi tanatsaye takasayin komai jira kawai takeyi taji yakushin berayen domin tunda take aduniya bata taba ganin beranda yayi girman koda Dan kaza ba banlantana kuma akuya Shiru taji tsayin mintuna ahankali tasoma bude idonta bataga komaiba tawaiga ko ina bakomai ahankali tasaukarda karamar ajiyar zuciya"" tayiyu bakomai bane kawai kallonda tayi dazune kaset din horo shine takejin tsoro""" Batareda wani kokonton tunanin taba takarasa dakin kawaidai saitaji jikinta yayimata ba dadi"" fitowa tayi takoma bangaren Usman tayi wanka tayi sallah""" sannan tayi kwalliya duk da bawata kwalliyace tayiba Dan jikinta jitakeyi tamkar anlikidamata shegen duka"" Bayan tagama shiryawa cikin kananun kaya Riga da sket""" masu karamin hannu"" tadauko Karamin hijab fari tasaka"" yar karamar fuskarta tafito tayimata kyau"" saukowa tayi kasa wajenda tabar"" kaleed"" Yana zaune kasa kusa dashi wadansu kadan karune manya"" masu katon kai kowanne daya girmansa yakai girman tsarii idanuwansa jajir tamkardai nawadan cen berayen""" cikin daga murya tace kaleed bar wajen nan""" tanarufe baki wadan nan manyan kadangarun suka soma keta wata muguwar dariyaa "" wacce ta karade dukan falon"" shikuwa kaleed sam baijitaba saiwasa yakeyi dasu yana dariya""" jikin ameena yasoma bariii tasoma ja baya ganin suna nufo inda take "" daidai shigowar Usman"" aidagudu taruga tafada jikinsa taboye fuskarta"" Cikin firgici yayarda jakar hannunsa yana tambayarta lafiya meenal?? Menene yafaru"" dahannunta ta nunamasa wajen kaleed shikuwa kaleed maganar babansa ce tasaka yadago kansa dasauri yadauko Dan kadan garensa naroba mai batir yarugo yana oyoyo papa"" jikin mahaifinsa yashige Usman yashafo kansa da hannu guda Sannan yamaida kallonsa wajen ameena yace please meenal kidago kikalleni nigabadaya kintayarmun da hankali"" Shiru yaji batace komaiba yasake girgizata saiyaga ta langwabe dasauri yature kaleed gefe yadagota illaikuwa AMEENA tadade dasomewa""" Cikin sauri yakarasa jikin kujerah ya kwantarda itah"" dasauri yadebo ruwa yazo yaballe murfin robar yasoma yayyafamata"" Tasaukarda ajiyar zuciya ahankali tabude idonta zunbur tamike tasake kankameshi tafashe dakuka """ jikinsa yajawota murya araunane yace waimenene meenal Dan Allah kisanardani kinsan halinda zanshiga idan inaganin kukanki??? Har abada bazanso kizubarda hawayeba muddin inaraye Dan Allah kidaure kisanarsani menene dalilin kukanki ??? Cikin muryar kuka tace Yaya kadangaru naketa gani masu magana"" akusa da kaleed Usman yakalli kaleed shima kaleed din shiyake kallo Wanda tunda mamarsa tafadi yakuramasu ido yana makale da kadan garensa naroba Usman yayi murmushi yace meenal kadangaren robar kikewa kuka?? Inakin saba ganinshi dashi sai alokacin tadago daga jikin Usman cikin tsoro tsoro takalli kadangaren Tsayin mintuna tamaida kallonta wajen Usman tace wadanda naganifa manyane kuma suna dariya"" kaleed yayi charab yace mom nan ake karamasu gilma"" yamatsa wata yar kunama saigashi yayi tsayi yanadaga kansa tamkar kadangaren gaske""" Usman yace tokingani dama bakisan haka yakeba"" idan tsoronsa kikeji kibari na konashi damacen kece kikasiyomasa danni banason ire iren wadan nan Dakinsa duka kincikashi da Teddy waiduk kayan wasane bakisan gunki bane kike ajewa badole saida wadan nan zaiyi wasaba kwanaki inaganifa harda macijin roba kika siyomasa""" Ameena tasaukarda gajeruwar ajiyar zuciya tace wlh natsorata Yayana"" tashi muje kayi wanka kakwaso gajiya"" karan hancinta yalakuta yace bayan kintayarmun da hankali Ninadaukama nine na aikatamaki wani gungumen laifii harna tanadi kalar hukuncinda zanyiwa kaina""" Murmushi tasake taboye fuskarta cikin jikinshi tace rufamun asiri wanne laifi zakamun nikuwa aduniya Wanda zaisakani kuka"?? Nayi kuka lokacinda nake marainiya tunranarda na aureka bakinciki baisake tunkaroniba Wanda zaisa kabatamun rai hartakaini gayinkuka Inaji araina nagamayin kukan bakinciki aduniya Allah yasharemun hawayena yahadani da nagartaccen namiji Wanda kowacce mace zatayi gurin samun abokin rayuwa kamarka Ina mai addua kowacce mace tasamu miji mai kwatankwacin halayenka""" ido yakwalo yace daina zigani hakamana Kinsa nafarajina asama ina shawagiii karkisa kaina yafasu dayawa"" Tayi dariya gaskiya nafada baban kaleed Dari bisa daribakada makusa duka dabi unka irinna nagartattun mutanene Yaja hancinta yace kamaryanda kike nagartacciya ba kisani nayarda dakefiye dayandà nayarda dakaina kyawawan halayenki sune sukesakani karasonki Babu shakka ke yar ajannace"" cikin zolaya tace idan kadagamuñ kafarkaba""" yayi dariya yace aituni nadage kafar wlh meenal da aljanna ahannuna take dakuwa kullum sainabaki itah sama dasau goma Murmushi tayi tamike dagajikinsa yadago yana kallonta zaiyimagana tadorah Dan yatsanta saman labbansà tace ka Adana kalamanka. Harsaimun kwanta yanzu katashi muje kayi wanka kaci abinci kafin nan lokacin sallah yayi saikaje masallaci . Yamike yana murmushi yace tomuje Amarya dariya tasaki tajindàdin sunanda yakirata dashi sosai tanajin dadin yakiratà dasuñan Tayigaba yanabayanta zuwa bangarensa tahadamasà ruwan wanka wadanda sukasha turareñ wanka masu kamshi Tataimaka masa yarage kayan jikinsa yashiga toilet din"" tarufemasa kofa yana zolayarta waibazata tayashi wankanba saboda yadebo gajiya Aisha✍🏼 ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠ chapter 21 By Gentle Lady💃🏽 Dariya tayi tace hannuna ciwon kai yakeyi kaidai kagama kafito tayi maganar tana karasa rufemasa kofar toilet din Wajenda yake ajiye kayansa tanufa tabude tafitomasa da jallabiya"" tafesheta da turare"" wayarsace tasoma ringing Tadauko ganin sunan little sister akan wayar yasaka tadauka cikin fara a tareda sallama dayan bangaren aka Amsa"" tace la Anty kicehar yasauka Tayi dariya tace ah wlh yagidan yamaigida"" kodayake aibakibada sakon gaisuwa akawomun ba"" tace la anty yaya baifadamakiba??? Tace baifadamun meba ??? nasan dakince agaidani aidabai mantaba dasaukansa zaisanar dani"" kubrah tace afuwan matar Yayana takaina kema kinsan bazan rasa turo sakon gaisuwata agunkiba inajindai gajiyar jirgi tasaukarwa Yaya yamanta da babban sakona Tayi murmushi to ankarbi uzurinki dukansu sukasa dariya kubrah tace Anty ina my son dina"" tace hmm sarkin rigima aini sonake babansa yakwasheshi dakayansa yaturah makishi cen konahuta da rigimarsa"" Kubrah tace la Anty wlh kaleed baida wata kiriniya kamar sauran yara"" tace aidole kice hakan tunda shine naki""" ya amarci yakuma kasar"" Tanisa Alhamdulillah wlh Anty nayi kewar gida sosai "" Ameena tace yaushe akai aure dukafa wata biyar yanzu kice kinyi kewar gida bayankuma kinatareda rabin ranki """ Kubrah tace hmm Anty kedai ayita sha ani waidama haka aure yake kullum inason intambayeki Amman saiyakureni da kallo idan inawaya bahalin inyidan sirri Dariya tayi tace wannan ma sirrine zaman aure ba komai kikagani azaman"" aure hakuri zakiyi wannan itace ibadar""" tace hmm Anty bazaki ganebane wlh nihar gajiya nakeyi saikace agogo kullum babu Hutu Ameena tanisa tace nagane mana Amman azancenki bazan ganeba kubrah shilamarin aure akwai sirri acikinsa barganin ina mace yar uwarki kiyi tunanin sanardani abunda kike fuskanta tareda mijinki Kisani kowanne dan Adam dakalar tashi sirrinki ki adanashi kizama maikunya nisam irin wadan nan maganganun wlh kunyarsu nakeji menene amfanin kazauna kana fadar mijina kaza mijina kaza "" duk yanda mijinki yake kibarwa zuciyarki saikiyita hakuri watarana sai labari kodai kinason yasake aurene??? Cikin sauri tace la ah ah Anty Sam bahakan nake nufiba kawaidai inadauka kowama hakan yakeyi kamar nawa"" Ameena tasakeyin murmushi tace ah ah Aiyanda kikasan halitta akwai banbance banbance atsakaninsu hakayake ako ina akwai banbanci Tanisa nagamsu Anty kuma insha Allah bazansake maganar ba""tace yauwa Kanwata "tace Anty wai ina Yayana??? "daidai fitowarsa wanka"" tace ga shinan yanzun yafito wanka"" yanadaure da towel daya hannunsa yanarike da karamin towel yana goge ruwan jikinsa yace naji ana gulmata Dariya tayi tace bafa gulma mukeyiba"" yace tayazangane bayan inajinku kunata kus kus kus"" dariya takeyi harda kubrah Tace sister ce takira taji kasauka lafiya"" yanataje sumarsa yace ainasan itace Dan idan ba itaba babuwanda zaikirah wayana kidaga""" Aisaiki fadamata nasauka lafiya """ tace ainafadamata tace Allah yahutarda gajiya""" yace Ameen sai ayi sallama ayidaniko"" yayi maganar yanarike kunkuminsa dariya ameena tasoma tace kinga sister zamuyi waya anjima"" Usman yace anjimadai meenal saikace wasu yammata"" tokaratunfa wazai karani tuni ameena takatse kiran tunda tagano abunda zaifada Tace kai baban kaleed wannan saikasani jinkunya agaban yar Kanwata""" baki yatabe yace wayajiyo kitaso kishiryani yunwafa nakeji""" Wayar ta aje tana murmushi ganin yanda yayi maganar kamarwani yàro dangoye""" saida tashiryashi suka sauka kasa"" kaleed yanasaman kujerah yana gem da TV Saman dinner suka karasa tagabatar masa da abincin ita tarikabashi abaki saida tatabbatar yakoshi alokacin magrib takawo jiki yawuce masallaci itakuma taka she TV taja hannun kaleed zuwa sama sukai sallah""" Usman baidawoba sai bayan isha"" falo sukatsaya suna kallo saikusan shadaya sukahau sama lokacin kaleed yadade dayin barcii Bayan sunyi wanka suka kwantaa""tunda suka kwanta ameena taketa mugayen mafarkai"" har asuba""" batasamu barci maidadiba saida sukasake kwanciya bayan haske yafito Sai wajajen karfe Tara tafarka""" koda tatashi har angama shiryamasu break"" bayan sunyiwanka suka karya"" tashirya kaleed cikin kayan makaranta""" Zasu wuce yasheka dakinsa saigashi yafitoda kadangaren roba"" dagudu ameena takarbe tayi wurgi dashi tace mezakayi dawannan a skull kuma??? Yace mom anty dinmu dukana takeyi idan nayi sulutu"" gobene wani kadangale yashigemata ajiki tanata ihu taluga munata dariya shine danje danawa databugeni inli amatashi"""" yakai karshen maganar yana dariyaa Ameena da Usman masaida sukadàara tace aimaganinkà kenan"" inba shashancibà mezaisaka surutu amakaranta anacikin aji ana karatu Yace mom banikadai nake sulutuba" tace kodakai dawanefa kadaina sannan bakyau tsoratarda musulmi kasani Yace to ai itah ba musulma bace sai wannan karon Usman yayi magana yace kaiwaye yafadamaka??? To aibata saka kaya ilinna mom kuma idan tashigo aji bata sallama"" ameena tace umm kaga kuwuce zaku makara idan kabiyewa surutun wannan Tariko hannun kaleed din sukafità Usman yabi bayansu"" harwajen mota tarakasu""" saida taga tashiñsu tanadaga masu hannu sannan takoma cikin gidan tana turah kofar shiga tayi Arba da katon kadangaren yanaganinta yanufota"" cikin saurii saboda tsabar firgita maimakon tayi waje saitakoma cikin falon""" Kadangaren kuwa yatasomata haikan tuni sukafara tsere acikin falon! Aisha✍🏼 ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠ chapter 22 By Gentle Lady💃🏽 Zagaye takeyi tanaganin kamar zaikamota kuma haryanzu bakinta yakasa furta addua Sam tama manta dawata addua Tana tsaka dagudun siket din jikinta yatadeta tafadiii'' take tayuyo tafashe da kuka mai karfiii ganin kadan garen yana dosota idanuwanta ta tamke waje daya"" Muryar maitayata aiki taji tana sallama"" Amman batayi gigin buda idontaba""" mai aikin tamatsa inda take tace uwar dakina meyasameki Cikin tsoro tace kadangare bakiganshi ba gashinan gabana ! Tawaiga bataga komaiba saicen nesa dasu tahango kadangaren kaleed naroba yanata yawo""" Tayi murmushi tace uwardakina babuwani kadangarefa narobane kawai na kaleed shikuma zai tsorataki??? Cikin tsoro tsoro tabude idonta taduba bataga komaiba saicen tahangoshi Takurah masa ido"" tasaukarda ajiyar zuciya tace wlh tabawa biyana yaketayi cikin falon nan munata zagaye dashi""" tabawa tace kawaidai dankinsaka tsoronsa arankine kike ganin haka"" barikiga" tabawa takoma saitin kadangaren tana kallonsa "" tawuce aikuwa saiyabita"" tasaka hannu tadaukeshi tace kinganiko bawai yanabinki bane kawai haka na urarsa take tana aikine da inuwar mutum Ameena tasaukarda gajeruwar ajiyar zuciya tace Amman ya akai kikasan haka tabawa??? Murmushi tayi tace uwardakina kinmanta nataba fadamaki nayi aiki gidan gomnan garin nan""???? Babu kalar kayan wasanda banagani awajen yayan matansa shiyasa nisam basa bani tsoro duk da wadan nan kayan basuda amfani"" dama wadan nanne wadanda alhji yake siyowa kaleed rakumi maiyin labbaikallahumma labbai"" ko wadan nan Na urorin masu addua duk Wanda" kadanna dakalar addua rda zaiyi tashiga bandakine kota fita gida dakuma ta fitowa bandaki Haka wacce take da complete Qur'an kowace surah dakin danna tasoma karatu irin wannan ne yadace da yayanku tanan ne yaranku zasu iyah addu o.in neman tsari kuma su iya karatu idan sunabi ahankali Amman nagake Sam bakitaba kunnasuba saidai kullum kibarsa da macizai dakunamu"""" ameena tanisa hakika abunda tabawa tafada gaskiyane Tunfarko data nunawa kaleed son wadancen abun dabazaiso wadan nanba"" gashi yanzu yasaba dasu abune bai wahala yayarda akarbesu daga gareshi"" tabawa takatsemata tunani tace me za adorah uwar dakina???? Tace kiferah doya yau sakwara za ayi"" Ina ladidi batazoba yau"" ??? Tabawa tace wlh nabiyamata jikanta bashida lafiya saisama nayo saurii idan masu girkin safe basu tafiba juwaira saita tayani idan aikin yanada yawa Ameena tace ina tunanin sunwuce Amman jeki kigani"" tace to sannan tawuce anan tabar ameena zaune takurawa kadangaren Ido tana tunani duk da tanatsoronsa tanagani tamkar yana biyarta Aikuwa kamar jirayake tabawa tabar wajen yayo wajenta "" cikin zafin nama tamike"" ta cakumeshi tayi waje""" sai kalle kalle takeyi"" wani katon dutse tadauko tayarda kadangaren tahau dukansa saida tayimasa"" raga raga batir da injinin sa duka sukafita dagajikinsa gefe takoma tana maida numfashi tamkar wacce taidanbe""" tayi tsayin mintuna biyar awajen sannan tatashi takoma cikin gida Saiyanzu hankalinta yadan kwanta"" sama takoma tadauko wayarta tashige kitchen wajen tabawa Karfe shabiyu akadauko kaleed daga skull tun abakin kofa yacikaro da gawar kadan garensa tuni yayi wurgi da jakarsa yasoma tattare kadangaren yana kuka Yanda yake kukan harcikin gidan anajinsa cikin falon yashiga yanata kuka dakarfi tamkar Wanda akedukansa Tabawa da Ameena kusan taresuka fito suna tambayar lafiya??? Ganinsa dauke da tarkacen gawar kadangare yasaka ameena taja tsakii cikin fada tace karufewa mutane baki"" Yace mom waye yakashemun adangalena??? Tace uwarkace akan wannan zakadameni dakuka maza kazubasu ashara ko inzaneka Tsayinsa yayi tace bazaje kazubasuba saina hadaka kaida kadangaren nawatsaku Shara tayi maganar tanayowa wajensà Yakwatsa ihu yayi waje dagudu yana nabani nabaniii gudu yake yana waigenta yaga kotakusa kamashi yanafita da itah da tabawa saida sukayi dariya Danyanda yake kiran yabani kuma yanakuka yana waige sai abun yabaka dariya""tabawa ta tsagaita da dariyarta tace waiwaya kashemasa kaya??/ Tace nice wlh tabawa haka kurum Abu saitsoratani yakeyi idan baiyi hankaliba gabadaya kayan wasar wlh saina cinnamasu wuta Kamar yasan inatsoron wannan shegen kadan garen"" kullum yana nan makale ajikinsa ainayi maganin abun tayi maganar tana shigewa kitchen tabawa Tamara mata baya"""" Kaleed kuwa wajen yakoma yayi zaune akasa yarungume kadan garensa yanata kuka""" yanasharar majina Karfe biyu Alhji Usman yakunno hancin motarsa gidan " idanuwansa suka sauka akan kaleed dayake kwance akasa yana barcii Baikaiga inda ake aje motociba yatsaya yàfito dasaurii yatunkari indayake barciyake sai Jan ajiyar zuciya yakeyi alamar yasha kukaa Aisha✍🏼 ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠ chapter 23 By Gentle Lady💃🏽 dukawa yayi yadaukeshi"" aikuwa yanajin antabashi ya zaburah yakwallah kara mom kiyi hankuli wlh inason adangalena""" idanuwansa arufe yake magana"" Usman yasharemasa hawaye yace bude idonka nine jin muryar dadyn sa yasaka yabude idonsa Yace yi shiru kadaina kuka wayadakeka"" ??? Yanajan ajiyar zuciya yana kuka ahankali"" yace mom ce takashemun adangale"" yayi maganar yana nuna masa""" yakalla yace toyi shiru bari kuka zansiya maka wani yaduka yadauki jakar makarantar da kaleed yayar yanufi cikin gida Ameena tana cikin falo" taci kwalliya""cikin wani tsadadden less tahakimce saman kujerah tanajiyo maganarsa da kaleed suna shigowa tasha toka tadauke kanta gefe "" kaleed yanaganin haka yasake makalewa jikin dadyn sa""" Usman yalurah dahakan murmushi yayi sannan yayi sallama "" ta amsa kawai batasake cewa komaiba Yace yaukuma mom hardani fushin akeyi dani ??? Yanda yayi magana batasan sanda tayi dariyaba saikuma tadaure fuska ta harari kaleed tace bance karkasake dawoda wannan shegen kadangaren gidan nanba??? Aikuwa yasake bare baki saida usman yarufe bakin yace yishiru sannan yakalleta yace waimeyasa mom yanzu kikacika fadane??? Dabahaka kikeba"" Tace hmm nidai kadaina cemun mom wlh dolensa yazubardashi ko inhado sauran kayan wasansa in cinnamasu wuta"" wannan kadangaren tsoratani kawai yakeyi wlh nayi danasanin siyensa""" Shiru yayi yana nazarinta sannan yamaida kallonsa wajen kaleed yace kaleed kaga mamanka tanajin tsoron wannan kadan garen kazubardashi shara kokanason mom tayi fushi dakai??/ Yayi sauri girgiza kai yace yauwa my son kaga itah tasiyomaka tunda yana bata tsoro aisaimu bashi kashi muyardashiko???/ Dariya yayi yace ah dady shima murmushi yayi sannan yasaukarda shi yace oya sheka kazubardashi shara"" yace to sannan yaruga dagudu Usman yakalleta yayi murmushi yazauna kusa da itah yace madam adan Samman murmushin mana"" wannan tamke fuskar yayi yawa kodai bakisan yanda kikai kyauba tamkar Amarya wacce za akaita gidan mijinta Dariya ameena tasomayi tana jefansa dakallo mai tattarreda soda kauna"" Waje yakaishi saida yakarasa dandakesa sannan yawurga cikin kwandon Shara Dasauri yadawo cikin falon wajen Usman yakarasa yace dady nayardashi saida nasake masa bulala tunda yana olatamun mom Usman yashafa kansa yana murmushi yace kabawa mom hakuri to yajuya wajenta yace mom kiyi hakuli ""ko kallonsa batayiba Usman yace kace Dan Allah bazansakeba yasake maimaita abunda Usman yace haryana kuka" yarike kunnensa kansa tashafa tace nahakurah Amman karkasake kansa yagyada to yajuya yace dad mom tahakurah""" Yadafa kansa Allah yamaka albarka"" yamike muje maza kacire kayan nan Tare suka Mike zuwa sama saida suka shirya sukasauko kasa sukaci abinci Daren ranar mugayen mafarkai da ameena takeyi duk akan wannan kadangaren ne tanaganinsa yatashi yahade kansa" ranarma batasamu wani ishasshen barciba saida tayi sallar asuba Bayan fitar Usman wajen aiki da tsoro tazauna cikin falon dazaran taji motsi takalla wajen dasauri"" idanuwanta sunasauka akan katon hotonsu dayake manne abangon falon saigani tayi suna motsi takesuka fara kyalkyatar dariya ba kakkautawa gabadaya suka cikamata kunne Hannuwa tasaka tarufe kunnenta tareda fashewa da kuka"" suma kamar hadin baki sukafara kuka aikuwa saigabaya hotunan dasuke falon kowanne yafashe dakuka Kukan yacigaba daratsa dodon kunnenta kowanne cikin murya daban daban""" take tahada gumi awajen sallamar tabawace tasaka ameena tadago kantaa ganin halinda takeciki yasaka tabawa saurin karasawa wajenta tana tambayarta lafiya??? Cikin tsoro tace bakiji dariyaba ??? Wadancen hotunan suketa dariya saikuma sukafara kuka Tabawa takalli hoton bataga komaiba tamaida hankalinta wajen TV dayake kunne tace to ai uwardakina cikin TV ake kukan Inajin kinsaka tsorono aranki shiyasa kike ganin hakan dama babu amfani saka wadan nan hotunan bakisaniba mugayen aljanu sunasamun wajen zamane agida idan sukasamu hotuna agidan koda rukiya za ayi sukan labe ajikin photon tayanda bazasu fitaba Mizai hana kisaka na ayatul kursiyu aiyafi wadan nan""" hawaye ta share tace taimakamun incire hakan kuwa akayi duka tacire hotunan harna dakinta"" Wasa wasa ameena tasoma ramewà tana lalacewà dagatsaye abunyasomà damun Usman"" yayi tambayar duniya tafadamashi meke damunta tace bakomai Tanemi yakaita wajen dangin mahaifiyartà"" baikawo komai araiba yakaita bayan yayimatà tsaraba maiyawan gaske"" kwananta hudu acen yaturah driver yadaukota yan uwa sunata kewarta Gidansu akawuce da itah ranar tashafirah da malam haryake tambayarta meyake damuntaa""" duk tarame saidai tace masa bakomai""" Sai dadare Usman yajedaukarta bayan isha I"" sunatafiya amota tanagefensa kaleed yajima dabarci"" takuramasa ido tana murmushi Ya murmusa yana kallonta yace wannan kallofa Amarya kamardai bakisanniba??? Murmushi tayi tasanne kanta kasa tanawasa dayan yatsuntà""" Usman saijanta yakeyi dafirah harsuka kaigida"""" .bayan sunshirya sukaci abinci sukai shirin kwanciya sunraya wannan Daren fiyeda Daren amarciñsu Sosai Usman yasamu yanda yakeso saikusan biyu sukai wanka suka kwantaa"""" karfe hudu darabii Usman yafarka agigice jin kiran sunansa DA ameena takeyi dasaurii yatashi yakunna wutar dakin abunda yagani yamatukar tayarmasa da hankali jinine yakefita tabaki da hancinta sare sare duk yabata zanen gadon""" Aisha✍🏼 ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠ chapter 24 By Gentle Lady💃🏽 Cikin kidima yayi kan gadon yana girgizata yana kiran sunanta dakarfiii Amman ina ko motsi batayi""" Daukarta yayi kamar jaririya yafito gidan tacikin na urah yashigo zuwa kasa saboda yayi sauri tunkafin yasauka yasoma kwalawa driver kirah Cikin barcinsa yaji ana kiransa"" firgigita yafarka yafito dasauri yana ganin halinda alhaji yakeciki Yakoma dasauri yadauko key din mota riga ahannu yafito Haryanzu usman jijjiga ameena yakeyi idanuwansa sunyi jajir tamkar gauta kadan yarage yasoma darzar kuka saidai kawai danyana namijine yanada juriya"" tuni driver yabude masa bayan motar yashiga da itah shikuma yazagaya yafita dasauriii zuwa hospital"" Tunkafin sukai yakirah family doctor dinsu yasanar dashi yace yana asivitin dan yana dutyn dare ne"" sunakaiwa yanabakin asivitin tareda wadansu nurse tareda gado""" yanayin pkng yadaukota akaturahta saman gado zuwa emergency Abakin kofa akabarshi Saikai kawo yakeyi tamkar yayi kuka"" tunda suka shiga da itah sukahau dubata saidai Ashe raiyayi halinsa"" zuciyarta ce tabuga!! Sosai yayi mamakin ciwon zuciya dahar yacita haka haryayi mata wannan illar Amman Sam shi baisan ciwon nata yakai hakanba""" Jiki asanyaye yafito dakin tareda sauran nurse "" Usman yana ganinsa yasoma tambayar lafiyar meenal"" Doctor yajikinta ???? Tasamu saukiko???? Dan Allah zan iyah ganinta?? Banaso narasata doctor haka yayita jeromasa tambayoyi tamkar maitabin hankali Gabadaya yabawa likitocin tausayi"" yace doctor bakace komaiba yajikin meenal din?? Yanisa yace tasamu sauki yadafashi saidai kayi hakuri Usman Koda kukashigo asivitin nan tuni Allah yakarbi abarshi""" cikin razana yadago manyan idanuwansa yadorasu akan doctor din Hannunsa yasaka yature hannun doctor dayake kan kafadarsa yayi cikin dakin dagudu doctor yabishi yana kiran sunansa Yanaashiga yajaye kyallenda aka rufeta dashi fuskarta tayi fayau tamkar tana murmushi tayi haske dukawa yayi akan guiwarsa yariko hannunta cikin nashi Cikin rawar murya yace yanzu dama tafiya zakiyi kibarni meenal duk wannan abun dakikemun na bankwanane take yafashe dakuka """ Doctor ne yadafashi yace hakuri zakayi Usman lokacintane yayi babu magani saimuyi mata fatar Allah yajikanta yasa tahuta"" ayanzu adduarka kawai takebukata Mikewa yayi yayi hanyar fita""" saidai yaji yarabke yafadiii dasauri yakarasa wajensa yanakiran nurse "" dagudu sukazo akadauki Usman akadorah akan gado take aka bashi taimakon gaggawa Ganin yafarfado yasaka akajona mashi Karin ruwa tareda allurar barcii "" driver"" yana waje baisan halinda uban gidansa yake cikiba"" saida doctor yasanar dashi""" alokacin ansoma kiraye kirayen asuba" wayarsa doctor yadauko aka Kira hajiya akasanarda itah""" Karfe bakwai darabi yamata acikin kaduna tuni labari yakai gidansu ameena"" mahaifin Abdul da Abdul suna asivitin Tuni akadau gawar ameena zuwagida dangin ameena saidai sukaji mutuwar kamar dagasama Koda yafarfado hajiya da Hafiz sunakusa dashi hawayene yasoma sauka gefen idanunshi hajiya tace sannu babangida"" Runtse idonsa yayi yace mom tatafi tabarniko??? Tashafo kansa tace addua zakaimata babangida lokacintane yayi""" Yanisa inason ganinta kicewa Hafiz yakirah doctor"" takalli Hafiz tace yakirashi yace to tareda juyawa Abdul yadawo kusadashi yadafa kansa Amman yakasa cewa komai"" yana tausayin abokinsa danyasan yanason ameena sosai Doctor yanazuwa yace badamuwa yana iyah zuwa"" taresuka fito suka dunguma"" saigidansu Ameena sunsamu har anyimata wanka""" Usman yamatsakusa da itah yayi mata addua tare akai mata sallah Tatara mutane sosai akakaita makwancinta""" Sam babu Wanda yatuna da kaleed saibayan da hajiya takoma gidan tasameshi yanata kuka sosai ta tausaya masa""" Saida akai sadakar uku kubra tazo tareda mijinta"" itakanta tasha kuka datasamu labarin"" Usman yakoma shiru shiru dagashi har kaleed sunrame danbasacin abinci sai hajiya tayi dagaske Bayan wata biyu darasuwar Ameena zuwa yanzu Usman yafauwalawa Allah lamarinsà"" Yakoma wajen harkokinsa Amman haryanzu baikoma daidaiba Hajiya takoma tareda kaleed hannunta saboda haryanzu yaki kwantarda hankalinsa""" Kwance take tanajuyi cikin barcinta"" zunbur tatashi "" tasoma dube dube mafarkinda tayi kamar almara"""ihun murna tayi tamike yauzataga handsome dinta towadanne irin kayama zatasaka tarasa inda zatasaka ranta danjin dadi Mikewa tayi tafada wanka"" agurguje tayi wanka tashirya cikin atamfa takawo hijabinta tasaka harkasa""" Wayarta kawai tadauka tafita unguwar kowa yayi mamakin ganinta da hijabi akafa take tafiya tayi nisa da unguwarsu sosai wata motace tayo cikinta sauran kadan tabugeta tayi gefe dasaurii Amman dukda haka saida yasameta aikuwa tafadiii kiiii yatsaida motarsa yafito dasauriii dasauriii yana furta innalillahi tadago takalleshi tuni tawashe hakorah tunawa dazancen *hatsabibin boka* yasa tayisaurin dukadda kanta gabanta nafaduwa Muryansa maisanyice taratsa dodon kunnenta sannuko inafatardài bakiji rauniba??? Kaitagyada masa tamike tana karkabe hijabinta"" yakuramata ido takeyaji Sonta yashiga ransa talurah da irin kallondà yakematà dadi kamar tafasa ihu arantakuwa tana aiyanawa ashema yafi kyau afili Aisha✍🏼 ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠ chapter 25 By Gentle Lady💃🏽 Muryansa tasake katsemata tunani yace inazakije yanzu??? Cikin sanyin murya tace mamana ta aikeni inyomata cefane"" yayi murmushi yace to idan bazaki damuba muje mana kisiyo daganan sainakaiki gida nabada hakuri Tadan waro ido tace hakurin mezaka bayar nifa banji ciwoba"" yasake gyara tsayuwarsa yace duk dahaka sainakaiki gida daganan sainaga waje aiko ??kobakyaso zumuncin mu yadorene?? nalurah kinaso kidatseshi iyah nan"" Munmushine ya subuce akan fuskarta tace waceni aiban isah ba Amman naga kaima kanada uzuri kawai kabarshi nagode zanhau Dan adaidaita"" harararta yayi cikin wasa yace tozanga yanda zakihau Dan adaidaita gani kusa ashekuwa yau akwai rigima Tace la abunfa duk baikai hakaba"" nayarda muje Amman idan mukaje unguwarmu nesa dagida zaka ajeni"" yace najidai muje Dakansa yabude mata gaban mota sukashiga yaja yasoma tafiya kifa nunamun wajenda akesiyarda kayan miyan"" batareda takalleshiba tace kana cikin legos kace bakasan inda ake siyarda kayan miyaba""" Murmushi yasaki yace ashekuwa yauzamuyi tayayo agari idan harsaini zan kaimu wajen"nida nake bako saiyanzu takalleshi tace wai dagaske kake???? Yace todakumafa nayimaki kamada yan Lagos???? Tace ausu yan legos harwata kamane dasu???? Yace sosai aidakingansu zakiganesu kullum suna sanye da dangakallun kaya"" sannan Kuma basada Faraa gadukkan alamu kema ba yarnan dinbace""tace ya akai kasanhaka??? Yace dabi unki mana"" ke komainakima so nice Murmushi tayi maidan sautiii tace kaidai wlh kafaye zolaya!" Sunakawowa daidai wata kwana tace nan zakabi""" tayita nunamasa hanya harsuka kawo Karyafa tasheramasa dankuwa bata tabazuwa siyen kayan miyaba"" toyanzu idanma tafita batafitoda ko asiba"" karfa asirinta yatonu yagano karya tashekamasa jitayi yabude mota""" zatafita yayi saurin dakatarda itah yace dame dame za asiyo??? Cikin rawar murya tace komaima Kaitsaye yawuce wajen maikayan miyan dayake inyamurine yace yahadamasa kayan miya"" na dubu biyar komai ahada""" Nankuwa akahada komai harda cucumber da kabeji dasu carrot" saida yanuna mata yace dubakiga ko akwai abunda babu asiyo"" tace komai akwai sannan akazuba bayan but sukakoma Tace kayan miyanfa sunyi yawa"" yace to kibawa wani idan sunyimaki yawa"" kidai nunamana hanya karmu bace"" Dariya tasoma kai malam akwaika daban dariya wlh"" takasan ido yake kallonta tana matukar burgeshi sosai"" yace basunana malam ba sunana Usman" Ido tawaro tace sunan uncle dina"" yace dagaske kenan nima nazama uncle" dinki""" tace sosaima Yanda sukeyin firah hankali kwance idan kagansu saika dauka sundade dasanin juna""" Suna kawowa unguwarsu tace ajeni nan zankarasa"dakafa Batareda yakalletaba yace babu amfanin zuwan nawa kenan tunda banga gidaba""" Ahakan tanuna masa gidansu""" yayi hon maigadi yahangame masa kofa yakutsa kan motarsa kamar wani dangida""" bayan yatsaya da motar"" yajuyo yana fuskan tarta yace gashi harmunkawo Amman bakifadamun sunankiba""" Naga abun yar rowar sunace""murmushi tayi taboye fuskarta cikin hijabi tace sorry aiban isah nayiwa uncle rowar sunanaba""" Yamurmusa yace nifa banyarda da uncle din nanba''' tarausayarda kai tace saime???? Yace aboki daganan kuma saiyayi shiru yana kallonta yanadariya kasa kasa Murmushi tasakeyi tace bari nashiga gida kar mom taga nadade""" yaduba agogon hannunsa yace shikenan ataimaka abani phone no""" Wayarsa yamika mata afuskar wayar PIC dinsane da Ameena kaleed yana tsakiya""" talurah da pic din saikawai tawuceshi tasaka masa Tamika masa Tace katsaya koruwa kasha""" ah ah inasaurine wlh akwai abunda nazoyi gobema zankoma Amman zansake zuwa gobe saimu gaisa"" Tabude motar tafita"" kayan miyar yafitomata dasu tabawa maigyaran fulawa tace yashiga dasu cikin gidan Sukai sallama tasake masa godiya tawuce yace amm jimana"" tajuyo ciikin wani salo Wanda yakusa sumarda Usman da ido tamasa akamar menene??? Yace sunan???/ Tadan dafe kai sorry namanta lubabatu tanafadàr maganar tayicikin gidan Usman yabita da murmushi wani sanyi""yaji yanaratsa dukkan sassan jikinsa rabonsa dayaji farinciki haka tunranarda meenal tabar duniya Murmushi yayi yashiga motarsa akabude masa get yafita Sam baiso zuwa legos dinba Ashe arzikine yake kiransa aransa yake ayyana hakan Tanashiga tasamu mom dinta tanadubà kayan miya""" tanaganinta tace lubcy wadan nan kayanfa??? Batareda takalletaba tace kiyi amfani dasu wanine yasiyamun tawuce bangarenta Mom dinta tajidàdi aranta tana adduar Allah yasa saurayintañe dantamatsu lubcy tayi aure Tanashiga daki tacire hijab tawurga akan gado tasoma tikar rawa tana murna harda ihu wayartace tasoma ringing tadauko dasaurii ganin sabuwar nomber tasan shine takidagàwa hartayanke akasake kirah batadaukàba saida yasake kirah tadauka cikin yanga kamar yanaganinta ta amsa sallamarsa sannan tace waye Aisha✍🏼 ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠ chapter 26 By Gentle Lady💃🏽 Murmushi yasaki maidan sautiii yace nashiga tara yanzun har ammanta dani ba aje ko inaba anya kinason zumuncin nan yadaure kuwa""" Gabantane yafadi karfa garin jan ajinta ta lalata komai""" tayi saurin taran numfashinsa tace bahaka bane uncle kaga aibansan nomber nakaba kuma kasan waya yana sauyawa mutane murya dat way banganekaba!! Amman kayi hakuri Ajiyar zuciya yasaukar wacce har lubcy tajiyota yace najisanyi araina"" itama murmushin tayi"" sukataba firah daganan sukai sallama Lubcy tamkar tazuba ruwa akasa tasha Dan Murna"dole"yau taturàwa *hatsabibin boka* kayan aiki nagodiyà!""" daren da itah dashi kasa barci sukayi kowa yana tunanin dayansa Usman jiyake tamkar kirjinsa yafaso zuciyarsa tafito saboda tsabarso nda yakeji nata yanahudashi""" Kwance take cikin dakinta tana danne danne dawaya saiga kiran Usman yashigo"" da murmushi tadaga tareda sallama daya bangaren ya amsa"" Yace gani akofar gida"" tawaro ido harkazo??? Harararta yayi kamar tana ganinsa yace dolekice harnazo danke bakidamu da niba nida nadamu dake darenjiya kasa barci nayi""" Tarike baki yihakuri uncle bawai haka nake nufiba ganinan fitowa"" takashe wayar akahau safe safe da feshe feshe saigata tafito das da itah tasaka hijabinta tafita""" mom dinta tanacikin falo zaune tace mom nayi bako kibawa kande kayansha takaemasa muna falon bakiii Tawuce abunta" yanajingije jikin motarsa yakurawa kofar gidan ido yanaso kawai yaga bullowarta"" kirjinsa sai harbawa yakeyi dasauri dasauri yakuramata ido yanda take tafiya tamkar hawainiya komai nata tsaf Kamar yanda yaraja.a akallonta itama haka shigarta yau Tayimasa kyau yau kananun kayane ajikinsa sabanin jiya dayasa manyan kaya idan kaganshi wlh koda anrantsemaka bazaka yarda yatabayin aureba sai idan kaganshi da matar kakuma tabbatar lallai itace Damurmushi takaraso inda yake tagaidashi"" tace karaso ciki sukajerah harcikin falon bakin"" tazauna nesa dashi suka gaisa""" yace badadewa zanyiba zuwanayi kawai mugaisa zanwuce Sam bataji dadiba Dan fuskar tama. Tanuna hakan cikin sanyin murya tace sai yaushe kenan?? Nasan dakyarne idan zakasake dawowa legos tunda bawajen zuwanka bane Yayi murmushi yanawasa da key din motarsa yace zancen baya kikeyi aiyanzu zuwa legos yazama dole dankuwa nayi babbar mantuwa acikinta Tace mantuwa?? togashi baka fitaba kakoma kadauko mana"" murmushi yasaki maidan sautiii yace kinaso ayimun ihu ace nasaci abunda banawaba!! zandauka Amman bayanzu zanjirah har abun yaxama mallakina Tace inamaka fatan alkhairi""yace nagode daidai mai aikinsu tashigo dauke datire cike dakayan motsabaki na marmari dakuma danbun nama"" saida ta aje taduka tagaisheshi """ Ya amsa cikin skin fuska"" zatafita yakirata kudii yaxaro cikin aljihunsa zasukai dubu goma yabata"" taki karba saida yamatsa mata sannan takarba tayi godiya"" Bayan tafita bajimawa yaduba agogo yace yakamata intashi haka"" karnayi dare ahanya"" gashikuma ban gabatar maki dakainaba"" Nasandai bakimanta sunanaba"" inaxaune a kaduna yanzu haka anan nake tafiyarda harkokina Amman iyayena akano sukeda zama Mahaifina Allah yamasa rasuwa inada kanne biyu kubra tayi aure sai Hafiz nataba aure karkiyi tunanin ni saurayine fuskarsa cikin murmushi yafurta hakan"" Yanisa Amman Allah yadauki abarsa tatafi tabarni dayarona daya kaleed tuni idanuwansa suka koma jajaye yace inasonsa sosai fiye dakomai arayuwa banajin zanso wani Abu samadashi Idan naganshi yana debemun kewar meenal azuciyata"" banason abunda zaitabashi komai kankantar abun" wlh lubcy yaron tausayi yakebani Yanzun yana hannun mahaifiyata "" inason narikajiñ dimin jikinsa akusa dani nasan mom bazata banishiba tunda bansan yanda zanrika kuladashiba aganinta zanraba hankalina gida biyu Shine nakeson nayi aure" kozansamu wacce zatakula damu dannikaina inabukatar kulawar""" yadago yakalleta yace kinji takai taccen tarihina aranta tace duk nasan wannan""" Afilikuwa tace Allah sarki Allah yajikanta""" yace Ameen toyanzu mekikace??? Tadanyi yake tace nikuma mezance???? Yasake gyara zamansa yace tomenene amfanin sanardake tarihina??? Takada kafada maybe kasanar danine as ur friend""" """ yace ya inatubka kina warwarewa"" dariya takwacemata ganin yanda yayi maganar Yace dolekimuñ dariya danbakyajin abunda nakeji gamedake""basaina tsaya kwanakwanaba agaskiya lubabatu tunda naganki naji nakamu dasonki Sobana wasaba""" kuma aurenki zanyi bansaniba kozaki iyah aurena amatsayina nawanda yataba yin aure yakai karshen maganar yana kallon fuskarta Tadanyi Jim yace please lubcy"" tarausayarda kai tace tokabani lokaci inyi shawara"" yayi saurin tarar numfashinta yace yanada kyau hakan amman nanda gobeko???? Tawaro ido gobe kuma??? Nanda satidaya dai"" bakiyabude cikin mamaki yace um lallai dasaurana bansamu shigàba""bari nasamu wajen zama a legos Dariya tasoma tanarufe bakinta tace lala nina isah nafurta hakan ayihakuri to abani nanda kwana uku"" yace biyudai koshidai sainakai zuciyatà nesa danzata iya bugawa!! tace to abarshi biyun . Yace yauwa amman please karkice baxaki aurenibà"!! Danzan iyah shigawani halin"" tayi murmushi saidai kajini kasha lemun mana tayimagana tareda nunamasa tirenda kedauke dakayan marmari""" Yace banajin zan iyah cin wani Abu harsainaji matsayina yayi maganar yanamikewa"" tace Amman kasandai banji dadiba acekayi bako koruwan gidanku baishaba Ahakan nasan iyah matsayinà"" yace yihakuri kinsan bansan yanda akeyin zancenba Ashe idan kazo dole kasharuwa Zansha Amman bayanzuba sainasañ matsayiña Aisha✍🏼 ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠ chapter 27 By Gentle Lady💃🏽 Tace shikenan"" saimunyi wayako"" yace ah Amman aizakimun rakiyaba ko anan zakibarni kamar saniyar ware??? Dariya tayi kai wlh kacika sa mutum dariya mujeto"" yace tofa dagayanzu kuka zanrika sa mutane. Nidai banceba baban kaleed""" sosai yaji dadin sunanda takirashi dashi har farincikinsa yakasa boyuwa yace nagodefa" daidaii get din gidansu tamasa sallama takoma gida"" Yabawa maigadi kayanda yasiyo mata yace yakaimata cikin gida sannan shima akabashi dubu goma"" zokuga bakinsa harkunne saikirari yakewa Usman shikam saidai yace kara da akayi Cikin gidan yashiga dasauri yana sallama niki niki dakaya"" ya aje gaban mom yace uwar dakina gashi inji alhaji"" takai bakin kofar dakinta tace barsu wajen mom tayi shigewarta Mom tabita dakallo aranta tace anya lubabatu batada aljanu??? Koda tafita gidan nan tana fara a Amman tadawo fuska yakunai yakunai kamar lawashin albasa"" idan yakwana Maigadine yakatsemata tunaninta yace yaunashiga uku uwardakina tana nema tamun bakinciki yanzun wannan Dan zinariyar tana nufin baiyimataba???. Hajiyarce tace wayafada maka ado?? Kaidai bakagani saika maganta tashi katafiii"" yace toya za ayi hajiya wayaki alhairi"" dubu gomafa tashi daya wlh hajiya kingansu a aljihuna yayi maganar yana bubbuga aljihunsa yacigaba tunda nake samartakata kawowa yanzu babu Wanda yataba mun kyautar dubu goma Keko dubu biyu ma duka alhazan dasuke zuwa wajenta shegiyar rowa tayimasu kanta aduwawu babuwanda yajeso yacire naira yabawani""" Amman wannan tunda naganshi nasan Dan albarkane""🤓 Dan Allah hajiya kirarrasheta kartace batasonshi Dama inada kwadayin dakwalen kajii kafin ayi auren na murmure"tace ado fisabilillahi kakoma wajen aikinka waikai meyasane kafaye shegen surutune uwa aku""" Yace saihakuri hajiya sai hakurii"" matsalarda akasamu kenan"" ranarda aka haifeni gidanmu anataron biki wannan hayaniyar tayan bukiii haya haya sanadinta tatakulo nakuda nayowaje Ashe surutun yanbikin yataba kakwalwata tun ina jariri idan nasoma dariya ina witsil witsil sai abun yabaki tsoro"" Yanbarka kowayazo saboda dariya sai yayi hawaye babana yakaini wajen likita yana tsammanin haukace takamani koda likita ya aunani yagano inada dauke da ciwon surutu kuma babu maganinsa harsaina cinye kaza Dari Tunda aka haifeni zuwa yanxu inakan lissafi naci kaxa ashirin dabiyar hargamida ta amarcina kinga koyanzu akwai sauran 75 tukuna inwarke Hajiya tace aikuwa baburanar dazaka warke dawannan surutun"" yace dainamun wannan fatar hajia kina raina surutuna kinsanfa magana jarice inaji ajikina dawannan surutun nawa zanyi arziki Tace ahakan? Aiwannan surutun bayan duka babu abunda zaijamaka"" aisaidai yajamaka tsiya"" um um hajiya raina kamafa kaga gayya"" inamai tabbatar maki sainayi govno agarin nan Hajiya batasan sanda takwashe da dariya "" auwal ne yadawo yayan lubcy yanata faman hon yaji shiru afusace yafito zuwa cikin gidan Yace haba ado waikai saiyaushe zaka daina wannan surutun Mara amfani nayi minti goma inabuga hon Amman kananan kanazuba Yace haba maigida toyazanyi banjikabane kasan bakyau akunkume baki saiyayi duyi""😆 Hajiya tanadariya tace waifa cewa yayi saiyayi governor agarin nan akan surutunsa"" auwal yaharareshi yace Na mahaukataba Ai wannan nangaba gadinma saiyarasashi "" yawuce fuuu kazokuma kabudemun kofa"" ado yawuce yana ta zuba ganinan zuwa karka gididdibani gida gida Lubcy tanashiga dakinta tayi wurgi dahijab tacije danyatsa tanakasa tanadabo kenan """ asheni banyi komaiba Dasake wlh kenan yafison dansa akaina???zai aurenine dannakula dayaronsa"!! Babbar magana nasan muddin yaron yanaraye lallai bazansàmu wata soyayya awajensaba Zairaba soyayyarsa gida biyune"" ina bazaitaba yiyuwaba dole naga *hatsabibin boka* yaudin nan Saikai kawotake acikin dakinta tanajiyo hirar ado da hajiya taja tsakii mstw surutun ado haushi yakebata idanyana magana bakinsa harkunfa yakeyi Tana zaune saman kujerah tana tunanin maganar Usman saigakiràñsa yashigo"" tadauka sukagaisa yakesanarda itah yakai Tayimasa sannu Allah yahutarda gajiya"basujima suna firaba yamata sallama yace ansoma kiran magrib zaiwuce masallaci sukai sallama yakashe wayar sake mikewa tayi akan kujerah batajima dakwanciyaba barci yadauketà Momdinta tashigo tasameta tanabarci saitafita karfe daya tafarkà taje tawanko idontà tadawo lokar kayantà tabuda tadauko karamin akwatin tabude tadauko madubin yana nan"" yanda ta ajeshi Saman gado tazauna tasahanñu tashafiii madubin tareda kiran sunan *hatsabibiñ boka* sau uku saigawani haske yashiga tacikin madubin saigashi yawashe *hatsabibin boka* yabayyana samañ kujeràrsa Cikin damuwa tace akwai Matsala sarkin bokayen duniya haryanzu tanakasa tanadabo""" yace yakikeso ayimasa??? Bataredà fargabar komaiba tace aturashi wajen mamarsa aganina zaifisàmun kwanciyar hankali darayuwa ataredani .inaso gabadaya danginsa sumanta dashi sukuma mantada mahaifiyarsa Inaso Usman yaji aransa baitaba haduwa dawata diyamaceba saini aciremasa son kowa adasa nawa""" *hatsabibin boka* yakeceda wata hatsabibiyàr dariya yace angama lubcy jeki kikwanta abunki kafin nandakwana 2 angama komai Bakaken aljanu sunagaisheki sunyaba dajininda kika aikomasu kamar walkiya hasken yafita daga madubin boka yabace tamkar walkiya. Lubcy tamaida madubin cikin jindadin bukatàrta tabiya takoma saman gado tayidaidai tañabarçiñta cikin kwanciyàr hankali. Aisha✍🏼 ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠ chapter 28 By Gentle Lady💃🏽 Bayan kwana biyu kamar yanda sukai da Usman saigashi yakirata"" cikin zumudi tadauka cikin rausaya" Tace aminci yatabbata agareka annurin zuciyata"" wani sanyine yaràtsa sassan jikinsa yalumshe idonsa sannan yabude Yace taredake ma abociya sassanyar murya Dafatar kina lafiya??? Tasake rausayarda kai qalau nake tareda tarin dinbin soyayyarka Yace wow Amman najidadin hakan sosai abisa dukkan alamu tarkona yakama tsuntsu kanta tagyada tace aitunima "" yace Amman shine baki sanar daniba kikabarni inata shawagi duniyarda bakowa acikinta saitarin furanni da ababen more rayuwa. Tace to aikuwa hankali kwance tunda kasamu jindadi aduniyar Yace kisani bazasu burgeniba matukar babu tauraruwa acikinta"" Zuciyata tayita jiran bakuwar soyayya wacce zata tallafeta zuciyata tazama fanko bakomai acikinta tana bukatar abokin zamanee Cikin zolaya tace to ai akwai kaleed"" gakuma marganyiya mamarsa"" shiru yayi kamar maison tunawani Abu daga bisani yace makotanku suke??? Cikin rashin fahimta tace suwaye??? Yace kaleed danaji kin ambata mana"" takyalkyale da dariya tace kainifa danka nake magana akai"" Yace danakuma??? Wanda zakihaifamun inmunyi aure??? Tace dankadai nayanzu yace Wayafadamaki inada da??? Yaushe harnayi auren dazan haifi da??? Wani sanyine yaratsa zuciyarta lallai boka yagama aiki saitace bakaine kasanardaniba kanada yaro mamansa tamutu Dariya yayi haryana rike ciki yace badainiba abunda nafadamaki kawai nacemaki nataba aure Amman fa ba azahiriba cikin mafarki mukai auren kuma munyi soyayya doguwa da itah Amman bata haihuba saitarasu tanarasuwa nafarka abarci wlh yanzu ko kamanninta bazan iyah kawomakiba kingakuwa shirmene Tasake shekewa da dariya tace hakane" yace yanzu idan kin amince zansanarda mamana anemamun aurenki Dannagaji dazama gauro abokina yayi aure nibanyiba nasan rashin auren ne yasaka naketa mafarkin nataba aure tace shikenan zan sanarda dad komai yace zakaji bayani yace yauwa tawan Sunkwashe tsayin wata daya sunabuga soyayya usman yamaida legos tamkar dakin kwanansa bayawuce kwana biyu baijeba Yasaba da ado maigadi sosai lubcy tagabatardashi ga mahaifinta a matsayin wanda zata aurah tasanardasu saurayine baitaba aureba Baban lubcy yace yaturo magabatansa"" ranarda lubcy tasanar dashi ranar yayiwa kano tsinke"" tunda mom taganshi sai fara a yakeyi sunazaune cikin falo yatankashe kafarsa kasa yanashan kankana Hafiz yana saman kujerah yanabuga game hajiya tace wainikuwa babangida wanne irin farinciki kakeciki nagatundazu saiwasar hakorah kakeyi??? Yasaka kankana cikin bakinsa yace hmmm mom albishirinki"" tace goro fari tasss tana gyara zamanta"" Allah yasa alkhairine Yasake murmusawa yasosa kansa yace sosaima "" tace tofadamun inji"" yace nasamo maki suruka mom Allah yakarbi adduarki nasamu wacce nakeso Aikuwa hajiya tarangada guda kai Amman najidadin wannan labari haba kokaifa duka abokanka sunyi aure Amman kai katsaya ganin garii inason nima insamu jika Yasunan surukar tawa??? Yana murmushi maikunshe dajindadi yace lubabatu saiyanzu Hafiz yayi magana yace Allah yasanya alkhairi Suka amsa da Ameen"" aikuwa hajiya tasanarda abokan mahaifinsa kasancewar yan uwan babansa bakusa sukeba"" Dan asalinsu buzayen Niger ne"" Cikin satii daya akagama komai anbiya sadaki dakudin angani anaso"" akasa bikin nanda wata daya""" ranar lubcy tasiye dabbobi guda goma ta aikawa *hatsabibin boka* Usman dakansa yaje Dubai yahadomata lefe Wanda ya amsa sunan lefe akwati talatin kowanne akwatin shake yakeda kaya sannan dasabuwar mota hul duk acikin lefen Lubcy saida tahada gagarumin farty gabadaya kawayenta sadiya.aneesa.rabiatu.larai.sajida"" suma saida kowaccensu tazo datata tawagar kawayen awani babban hotel sukayi fartyn kowannensu saida yagirgiza daganin kayanda akadirkowa lubcy amatsayin lefe Ranar sun gwangwaje sosai saikusan magrib suka watse"" Cikin watadaya lubcy da Usman tamkar suhadiye Kansu Abdul ma saubiyu Usman yana zuwa dashi wajenta Biki yakarato kowanne bangare sai shirye shirye ake kubra matazo da dankaramin cikinta ansoma hidimomi Usman yagyare gidansa an sake komai kuma anyisabon fenti Bangaren lubcy kusan sati biyu sukayi suna program event itakanta tasan takere sa a ta auri mijin nunawa sa a Bikinsu Na gogaggun yan boko ko ince yankarya Dan yanboko akwai karya kankanba danuna sudin wata tsiyane Ranar lahadi dubban jama a suka shaida daurin auren lubabatu da Usman akan sadaki million 1 Karfe uku motochin Amarya sukadauki Amarya zuwa kano wajen mahaifiyar Usman yankai Amarya censukà kwana tareda kawayenta Washe garii akawuce da itah dakinta ai kawayenta basu tsureba saida sukayi arbada aljannar duniya acewarsu Dan babuce kawai babu acikiñ wannan katafareñ gidan kowa sai santin gidan yakeyi saidare akawatse akabar amarya Daren Usman ya angonce zokuga ririta tamkar zaimiyarda itah ciki sosai takemasa ladabi hartakan mantar dàshi kowa muddin yanatare da itah Bayan wadansu watanni lubcy tafara gajiya dabukatarsà saitatsiri ciwon karya kofashin sallah"" lokacinne kubra tahaihu mace akasamata suna bilkisu hidimar kwana biyu tasaka lubcy tadan sarara Aisha✍🏼 ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠ chapter 29 By Gentle Lady💃🏽 Bayan wata uku lubcy tafara laulayin ciki ranarda doctor yasanardashi tanadauke daciki zokuga murna daga hajiya har Usman tamkar suhadiyeta tuni labari yakai wajen kubra Takirata tatayata murna taimata fatan sauka lafiya cikin sosai yake wahalda ita gakuma yawan kwadayi kamar manya"" Aikin komai tadainayi acikin gidan saidai taci takwanta saikuma Usman yasake manne mata da lakuwa kamar danyaye"" Cikin yana shiga wata Tara kafafuwanta suka kunburah komai bata iya yikobanza gatada sonjiki sai akagamu akadace Ranarda nakuda takamata akadauketa sai hospital tasha wuya Amman haihuwa tayi tsayinta gashikuma tagalabaita Likita yace dole Usman yasaka hannu aimata aiki aciro yaron domin dan cikin yawahala tareda mahaifiyarsa "" Usman hankalinsa yayi matukar tashi Saida doctor ya rarrasheshi yasaka hannu akashiga da itah dakin tiyata akaciro kyakkyawar beby maikamada Usman sak tamkar yayi kaki yatofar Bayan anyimata dinki aka kaita dakin Hutu"" sosai Usman yakejin son jaririyar harcikin ransa take yadauki waya yasanarda hajiya da Abdul da kubrah yakirah gidansu lubcy yasanar Ranar duka sukazo saigashi ancika asiviti makil damasu dubiya har makotanta saboda tanada mutane sosai"" satinta daya sannan aka sallameta kaitsaye Lagos akawuce da itah"" aikuwa Usman yamaida Lagos garinsu kullum yana zaryar hanya Anasaurah kwana biyu biki kubra tazo""" sosai sukejida yarinyar ranar suna akaradamata suna labila Usman gida biyu yakasa kansa"" bayawajen aiki baya Lagos aikuwa tanayin arba in akahadota tadawo Sosai tadan huta da jarabar Usman kwana biyu Amman ranar taraina kanta dankuwa saida yafanshi nakwana arba in datayi basatare danyagaji iyakar makurah Labila tayi wayonta sosai ko ina tanazuwa tanada shekara daya dawata bakwai aka yayeta"" lubcy batasake samun cikiba saida labila tacika shekara uku Shima wajen haihuwa saida aka fasata saboda wahalarda tasha yaron yamutu cikin ciki"" tunlokacin batasake samun cikiba Saida labila tacika shekara goma"" sannan tasamu ciki shima hallau tiyatarsa akai mata tace ajuye mata mahaifa dantagaji Amman badasanin Usman ba"" Katon danda akaciro mata shima kyakkyawa Amman labila tafishi kyau Dan ita ta fidebo kamannin mahaifinta""ranar suna akasa masa suna abdul-majeed sunakiransa majeed Yana isah yaye tayayeshi domain sun shirya wata tafiya tareda kawayenta "" tatambayi Usman duk da badason ransaba Amman bazai iyah musamataba ita tadauki nauyin tafiyar har aje adawo Sukayi shirye shiryensu ranar talata jirginsu yadaga zuwa charo satinsu biyu acen usman yadameta da azarbabi yace wlh tadawo hakanan badan tasoba dandama gudun hijirane taimasa tadan huta Ranarda sukadawo tsautsayi ya afkamasu akan hanya dukkansu sunji ciwo sosai bakamar lubcy dangaba gareta yaji chiwo sai alokacin akalurah dakarinda kejikinta yagirma tamkar bishiyar kuka haryazubarda Yaya Shiyasa batason Usman yakusanceta likitoci suka tabbatar sai anyimata aiki kuma Karin babbane danhaka zatafara dashan magani Usman kamar yayi kuka danyasan tashi takare dankuwa likita yace karya kusanceta saida suka kwashe watadaya hardasati sannan suka murmure Tass alokacin Duk hankurin Usman yakare Kawai yafada Neman auren wata suwaiba acikin kaduna take sosai sukeson junansu yasanarda hajiya bata tambayeshi daliliba tunda tasan yanada halin yin auren Tadaimasa nasiha akan yakwatanta adalci cikin sati biyu akagama komai harlefe Amman yakasa sanarda lubcy Dankunya yakeji yazata dauki maganar kenan baigodeba duk da hakurin datakeyi dashi danyanzu matsala tasameta zaigujeta kumashi Sam baida burin hakan Zaune yakecikin falonsa yana tunani wayar sa tasoma ringing kamar bazai dagaba saikuma yadauko cikin sauri yadauka danharta katse an sake Kira hajiya ce yadauka tareeda sallama ta amsa"" yagaida itah cikin ladabi ta amsa tace ina yaransuke Yagyara zamansa yace suna islamiyya tace hakane Sam na sha afa yaune asabar mamansufa???? Yace inatunanin barci takeyi"" tace toyajikinta??? Yace todasauki za ace"" Hafiz yana gida?? Tace yanzun nan Na aikeshi wlh Dama kiranka nai insanarmaka kamar yanda kabukata ansaka bikin sati biyu "" yasaki fara a kai alhamdulillahi Amman najidadi Tanisa Allah yasanya alkhairi yace Ameen tace babangida"" yace Na am tareda saita natsuwarsa tace inafatardai kasanarda lubabatu batun aurenka??? Shiru yayi yanasosa kai kamar munafuki yayi karya""" tace shirunka yanuna kenan baka fadamataba Cikin kunya yace ah hajiya wlh nakasa tunkararta da maganar kayanda nazodasuma suna falon baki na aje dazaran naso sanarda itah sainaji tabani tausayi Hajiya tace totunda tausayi takebaka kafasa auren mana"" idanuwansa ya kwalalo aransa yace kice inmutu kenan"" Cikin zuciya yayi maganar baisan tafito filiba hajiya tace wacce irin mutuwa duk wadanda suke zaune damata daya kaga sun mutune?? Yayi shirudai aransa yace hajiya bakisan halinda nake cikiba""" tace totunda har kaidin bazaka iyah hakuraba yazamar maka dole kasanarda matarka Amman muddin karufemata harsai randaurin aure kokuma taji ashanun tallah tokuwa liki za atono Aisha✍🏼 ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠ chapter 30 By Gentle Lady💃🏽 Yanisa shikenan hajia zansanar da itah "" tace yauwa kokaifa ai boye boye bashida wani alfanu ansan kowa yanada kishi Amman hakuri zatayi ai tunda mijinta yanada bukatar kari Yace zanfadamata insha Allah tace hakan yayi sunjima suna firah sannan sukai sallama yayi shiru yana kallon wayarsa shikam gabansa sai faduwa yakeyi Mikewa yayi yasauko dakinsa"" hawayayi zuwa bangarenta cikin falo yasameta kwance remote ahannunta tana cenza tasha tana ganinsa tamike da fara a Alhaji Kaine dakanka bayan kakirani inzo"" yayi murmushi bakomai aigani nazo yayi maganar yanasamun wajen zama kusa da itah Yace hutawa akeyi"" tace ah wlh kafin majeed yadawo kasanshi akwai Rigima jiya da dare damuna yayi dakuka kamar karamin yaro Yace todakumafa haryanzu bakimasa kaniba aidole yayi sakuwa dar taji agabanta Sam tama manta da anjuyemata mahaifa Kuma bazatayarda wani tsautsayi yasaka tasanarda Usman hakaba Dantalurah sosai yana mutuwar son yara gashi biyune kawai da itah" yakatsemata shirun tahanyar kiran sunanta Datago ta amsa cikin fara a"" yanisa dama akwai maganarda nakeson yidake"" tadanyi shiru sannan tagyara zamanta dandama kishingide take gahannun kujera Takalleshi inajinka alhaji"" yadanyi jim sannan yace kafin nacekomai inamai baki hakuri akan abunda zanfurta maki nasan bazakiji dadiba Amman kiyi hakuri wlh nadade ina kumuiniyar maganar dantayi nauyi akan harshena Yasake nisawa karkiyi zargin naraina kokarin da kikeyi akaina kodaya wlh najinjina maki hakaxalika ina alfahari dake Karki zargeni dawani Abu Dan Allah wlh haryanzu inasonki sonda bantaba yiwa wata mace makamancinsaba aduniya Lubcy dai tayi shiru tana saurarenshi haryakai karshe murmushi kawai takeyi yadago yakalleta murya araunane yace aure nakeson karawa kuma maganarda nakemaki harnasamu wacce zan aurah Nakasa sanardake ne tuntunii"" nasan kinsanni kuma kinsan lalurarda nake dauke da itah bazan iyah rike kainaba nasoyin hakuri Amman nakasa doctor yasanar dani akallah zakifi shekara komafi kafin ayimaki aiki Dan likitocin dasuke wannan aikin sunakan wani aikine tayiyu sugama kafin nan kuma ka idar aikin saikinsha magani akallah nawata biyar sannan Yasake kallonta idanuwansa sunkada jajir banaso na aikata zina abarda nakyamata tun ina saurayina yanxu dagirmana da Yayana bazanyiba dankuwa zansiyawa Yayana halaka dahannuna dankuwa duk abunda nayi nima sai anyimun Nayi kokarin fara azumie amman duk dahaka nakasa Amman kiyi hakuri kinji matata yayi maganar yanariko hannunta ga mamakinsa saiyaga tatintsire da dariya Bakisake yake kallonta tace wlh baban labila kasakani dariya yanzu akan wannan maganarne kakasa sanardani?? Tundazu kakeson fadar abudaya Amman kakama kwana kwana kawai kacemun aure zakayi zanhanakane??? Nasan mata sunada kishi Amman nisam banadashi kuma bawai Dan banasonka bane kodaya Amman kasani dole inhar soyayya tacika soyayya kaso abunda masoyinka yaso kome kakeso aduniya komai muninsa gareni inhar kafurta kanaso tonima dole naso abun Kaddarama abun bakine aguna inhar yazama fari awajenka nima yazama tuntuni nasobaka wannan shawarar tunda nidai banada jimirin dauke lalurarka kuma sainaga Kamar zanyi shishshigi sainakama bakina Amman bakomai awajena kasaki ranka Allah yasanya Alkhairi tsuru yayi yanakallonta Baisan sanda yarungumetaba yafara sunbatarta ganin yasoma fita hayyacinsa yasa tatureshi tace kamantane Karamin Tsaki yaja yace wlh kamar namutu nakeji tanisa cikin alamar tausayi tace tomezaihana asabikin kusa kusa kozaka samu abunda kakeso Yace ah sati biyu akasaka bakomai zancigaba dahakuri zuwa lokacin""" tatausaya masa matuka yace nagode sosai lubcy hakika ke Yar aljannace inama sauran mata zasuyi amfani da shawarata surika hakuri idan mijinsu zaikara aure Dazasukoyi irin halayenki nakwarai da duniya tahaska"" murmushi tayi nidai kadaina zugani wannan zuzutawa haka Dariya yayi aikin chan chantane"" yasake riko hannunta nagode sosai tace bakomai yasunan kanwar tawa??? Cikin nunajin nauyi yace suwaiba""😌 tace wow suna maidadi yakamata kafin akawota anunamun photo n kanwar tawa yadan Sosa kai yace bari nadauko wayata kigani Yar duma dumace kamarke Yayi maganar yana mikewa tace bansaka wahalaba??? Yace kodaya daganan kobirnin sin kikaturani dakafa zanje saidai indade bandawoba tasa dariya ko maigidana ashedai kanaji dani ??? Yace kamar kwai kuwa yawuce Tabi bayanshi damugun kallo yanafita taja wani dogon tsaki aranta tace wai aure???🙄 To ayi auren mugani ai wlh danabarka kakusanci wata matar amatsayin matarka nafiso kamutu Inaruwana da lalurarka saidaifa kaje kayi zina komata Dari zakanema ni lubabatu bandamuba kazantarda bakaganiba tsabtace😏 Amman bazan taba yarda kakawo wata acikin gidan nanba Dan nawane danida Yayana"" bazantaba bari Yayana susamu yan ubaba Karuwai ka ajedari awaje aidama akan abun zakayi aure nikuwa inamai tabbatàr maka bazaka samuba hmm namiji munafukiñe jiyanda yakewani lallaf yadauka salihar mace yakawo agidansa baisan kububuwa takeba cinnaka bakasan nagidaba zumanake maizaki ammankuma gaharbi harbinama yazarta Karin maciji dafii Afili nake mumina Amman azuciyata nafikowa sharri jin motsin dawowarsa yasaka lubcy tadaidaita natsuwartà Yashigo da sallama ta amsa"" kusa da itah yazauna yajawota jikinshi yakamo mata pic din tana kallo Tace kai ammanfa kanwar nan tawa bakaramin kyaune da itaba"" yadan hararetà yaçe batakai kiba lubcy aranta tace kunji munafuki waya sàñima koharzagina kukeyi Amman afili saitace ko??? Yace sosaima yanda kikasan kyawawan fure haka nakeganinki wai anyama wani yataba fadamàki kinada masifàr kyau?? Dariya tayi cikin nuna alamun jindadi tace ah ah Amman gashi aikai kana sanardañi Aisha✍🏼 ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠ chapter 32 By Gentle Lady💃🏽 Dasauri tamike zuwa bandaki yabita da kallo tunda suke tare bata tabayin wanka aLookacinda suka taraba Koda yace tatashi tayi wanka cewa takeyi bayanzu zatayiba saida safe idan suntashi sallah Amman yanzu dabama Kusan tarta yayiba tajeyin wanka yanatsaka da tunaninsa tafito daure da towel Yasake binta dakallo yana hadiye yawu shikam baisan yawan bukatarda yakeda itah ba baitabajin ya gamsuba komenene dalili Ruwan jikinta tadan watsamasa yadago yana kallonta gira tadaga masa tace tunanin me kakeyi??? Yace kekanki kinsan tunanina bayawuce matsalarki wlh kokadan banji nasamu natsuwaba hartausayin kaina nakeyi Kusa dashi tazauna tana goge kanta tace hakuri zakayi basaura kwana sha huduba aikamar gobene zaka angwance ni idan kayi auren nayafemaku kayi wata daya dakinta kasamu kamore amarcinka Cikin alamun nunajin dadi yace dagaske kikeyi??? Talunshe ido tabude kadaina shakka ko kokwanto akan maganata babu abunda bazan iyaba indai akankane"" fatana shine kasamu abunda kakeso Inason ganinka cikin kwanciyar hankali yalumshe ido yabude yace nagode matata farincikina Tace karka damu kaje kayi wanka ko yace hakane yamike yadaura towel yashiga toilet dasauri tadauki wandonsa tareda abunda kecikin kwalba lakame da towel dinta tafita zuwa dakinta Tanazuwa ta ajesu waje daya tasaka kayan barci tafito zuwa dakinsa koda yafito yasameta hartakwanta wasu kayan barci yasaka shima yahau gadon Yajawota jikinsa tareda saukarda ajiyar zuciya sosai yanason jin duminta Amman tunsanda batada lafiya batasake hada shinfida dashiba kullum dakinta take kwana sake jawota yayi cikin jikinsa barci maidadi yadaukeshi tareda mafarkai masu dadi washe gari saida yasake wanka kafin yaje masallaci Bayan kwana biyu yashigar mata da kayanda yasiyomata tanata murna tanayaba kayan"" yadaukesu sukaje kasuwa yace kowa yazabi kalar abunda yakeso Sunkawo kaya sosai duka yabiya kudin Dan sainan nan yakeda itah" tuni tasanarda kawayenta suzo ranar asabar maizuwa akwai fatynda tashirya Na musamman"" agidanta Sam bata sanardasu aure Usman zaiyiba Ankai lefe gidan Amarya kuma duk wadansu kudi da ake bukata ankai dagashi sai Abdul sukeyin hidimominsu saboda"" bashida wasu abokai"" Ranadai bata karya saida"" uwar diya taji kunya""yaune dubban jama a suka shaida daurin auren Usman da suwaiba akan sadaki dubu Dari biyar" Daurin auren yasamu halarta mutane sosai dayake Usman mutumen mutanene"" ango yasha farar shadda sai wasar hakorah yakeyi shikadai yasan abunda yatanada adaren yau Lubabatu ce cikin dakinta tareda kawayenta sadiya larai sajida aneesa rabi atu"" sadiya tace waini kince muzo gidanki Amman bakisanardamu komaiba kuma munga gida cike da alamun biki akeyi"" Tamurmusa tace biki akeyi kuwa"" larai tace bikin mene??? Tace aure dadyn majeed zaikara kusan tare suka hadabaki aure???? Tagyada kai tana shan lemu "" sajida tace tirkashi kuma kike zaune anan??? Takalleta tace tome kikeso inyi kinasone intada hankalina bayankuma mijina yanasona??? Rabi atu tace soyayyar banza ai wlh duk sonda danamiji yakemaki dazaran yakara aure zakizama photo"" aiyanzu yadaina yinki tunda yasamu yarinya bayankuma shine yamaidaki hakan Ta aje kopin hannunta tace ninasan mijina yanasona sosai"" kuma babu tayanda wata zatafini matsayi acikin zuciyarsa Sajida tasheke da dariya tace naga alama giyar soyayya batagama sakinkiba tokibude kunne kiji namiji dakike ganinsa tsohon munafukine bazaki gane hakanba sai ankawo matar Barinma ya tas tata yagano tafiki sweet hmmm sunanki sorry kinaji kinagani zakikoma borah agidan nan .takarewa gidan kallo kinga wannan gidan wlh kinagani zai gagareki zama Dake dayayanki gidan nan zaikoma maku tamkar kurkuku bari kiji yanda mukayi da dadyn ihsan lokacinda yakeson yin aure Sam bainunamun komaiba kamar yahadiyeni dama gayanda muke kullum sai riritani yakeyi da dadin baki Nikuwa ahaukana sainaga aisonda yakemun kamar baxaiso wata bayan idona ba"" saiban dauki matakin komaiba nayita rawar kafa har aka kawo Amarya Nikam sai lokacin nasan natabka babban kuskure na aminta da danamiji dansaboda kawai yamun dadin bakin soyayya Idan yanadakinta wlh ko motsinsa bakyaji saidai inshige daki inyita kuka saboda takaici sairawar kafa yakeyi inhar girkinta yazagayo Amman ranar girkina sainaga baya walwala bayanuna zakuwarsa Lubcy tace toyakikayi??? Tace hmm aisaboda naga wankin hula yanashirin kaini dare" kawai nakai sunanta wajen *hatsabibin boka* aka kadamun Yar banza hatta cikin datafita dashi aka narkardashi yabi mazubar ruwa Sukasa shewa suka taba rabi.atu tace wlh kinmun daidai"" aikishiya ba abokiyar zamabace mekike jirah kinsandai yanda kikashigo rayuwarsa danhaka idan kikatsaya wasa wata tashigo takarbemakishi Lubcy hmm kawai tace sajida tace kaikudaina wahalda kanku tasan abunda tataka"" lubcy takwashe da dariya tace kudai akeji mahaukaci yafada rijiya Kamar ance sudaga Kansu sukayi arba da labila tanarike dakugu takallesu dai bayan daya tace hmm wannan muguwar hudubar kukazauna kuna koyawa mamana duk danasan batada mugun hali Amman bazan shedetaba danzata iyah sauyawa Danzama damugayen kawaye irinku hatsarine garayuwar iyali "" lubcy tadago afusace takunduma mata zagii abunda bata tabayiba tace asheke shasha shace??? Anandin kinunamun abokin wasanki Wlh karnasake ganin kin shigomun daki waima tsaya labe kikemana ko??? Idanuwanta sunakawo kwallah tace komadai menayi wlh muddin matar dady wani Abu yasameta saina sanardashi gun boka kikezuwa lubcy tataso daniyar dukanta taruga dagudu tace kukuma kuji tsoron Allah inkuwa bahakaba kuyi mummunan karshe takafro kofa ganin tana niyar dankotaa Aisha✍🏼 ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠ chapter 33 By Gentle Lady💃🏽 Lubcy tadawo"" tanata sababi saida su sajida sukaita bata hakuri sukace ai kuruciyace zatadaina nan gaba"" Aranta kuwa tanatsoron shegen surutun labila tunda hartace hakan bamakawa zata sanarda Usman kuma zaiyarda da maganarta danbataimasa karya sosai tasan yana yarda da maganar labila Lallai kuwa yazama dole tayiwa tubkar hanci zata sanarda *hatsabibin boka* dawan nan tunanin sukacigaba da harkokin gabansu Yanbiki sukafara cika gida alokacin taiwanka tafita cikin mutane akafara jidoda kayan ciye ciye"" Karfe hudu nayamma akatafi wajen faty Wanda uwargida tashirya awani babban hotel namaza damata inda Amarya dakuma ango tareda uwargidansu agefe aka zauna saman dandamali Bayan anbude taro da addua akafara gabatarda shirye shirye inda maikida yayita wasa uwargidan Alhaji usman akan wannan katafaren biki data gayyacesu Aka umurci Amarya da ango sufito tsakiyar taro sutaka rawa haka sukafita anatakemasu baya Nan take akasaki kida tareda sowa""" lubcy tayi ruwan kudi tamkar dagasama suke zubowa sailiki takewa Amarya inda Usman shikuwa yakeyimata Kawayenta suma sukafara yimata likiii"" sosai masu kida suka kwashi kudiii"" tarokam yayi taro duk inda lubcy tawurga maganarta akeyi anayaba halinta Lubcy macece wacce ta iyah zamada mutane sosai tasan yanda take tafiyarda rayuwarta macece wacce tasan takan kissa dakuma kisisina Shiyasa har makotanta""suna sonta sosai" dakuma yaba halayenta"" basu suka tashi wajen Fatyn ba saida akasoma kiran margin sannan akatashi bayan anci ansha anyi katt Amarya anazuwa akasoma shiryata domin Kaita gidanta"" karfe takwas motocin daukar Amarya suka faka kofar gidansu Bayan iyayenta sungama yimata huduba akadauketa sai katafaren gidanta bangaren uwargida aka Kaita akabata amanarta taredayi masu nasiha Tacee bakomai ai kanwace niban dauketa kishiyaba aikuwa dazasu tafi har bangaren Amarya tarakasu kowayatafi dayabon halayenta Karfe goma kowa yawatse akabar Amarya agidanta tareda uwargida gidan yayi tsit Tasake wanka tadawo cikin falon tana zaman jiranshi zamanta babu jimawa Usman yashigo Yana yin arba da itah yasaki fara a yace haryanzu kinafalo bakyajin tsoro ina labila??? Tamike cikin fara a tace sunyi barci nimadai shinakeji natsayane inrakaka wajen Amarya karkashiga kaidaya Yace kamar kinsani bazan iyah shigaba" tace tomuje karage kayan jikinka kawatsa ruwa sainarakaka Amman yabanganka da kazaba Kansa yadan Sosa yace tana mota wlh namanta"" tace tokadauko bari nahada maka ruwan wankaa yace yauwa nagode yajuya cikin zumudi tabishida murmushin mugunta dakinsa taashiga tahadamashi ruwan wanka yadawo yashiga yawatsa tadauko masa kayan barci masu kyau Tafeshesu da turare yana fitowa yasaka kayan suka fita tanarike da plate da madarar shanu bakin kofar dakin tatsaya Tamika masa Yace yahaka bazaki shigo bane??? Ido tagwalalo ah ah kaikam damadai rakiya naimaka kagaisheta dai Tamika masa kajin yace tokebaki dauki takiba tace ainima nacitawa lokacinda aka kawoni wannan ta amaryace tasunbaceshi akumatu asha amarci lafiya tawuce abunta tana murmushi yabita dakallo cikin soyyya yana fatar Allah yabarshi da matarsa Baisan wanne irin so takemasaba dahartake iyason abunda yakeso duk abunda akeyi bisa kunnen suwaiba tagodewa Allah dayabata kishiya tagari Yashiga bangaren da sallama ya aje kayan hannunsa saman gadon yahau yaciremata mayafi yana murmushi Amarya ta ango murmushi tasaki cikin jinkunya Yace yaudai Allah yacikamana burinmu kitashi muyi alwala mugodewa Allah"" bamusu tamike domin dauro alwala saiga jinin al ada jiki asanyaye tafito Ganinta dayayi sai ahankali yatambayeta tafadamasa tanafashin sallah baice komaiba yagabatar masu dakajin sukaci saida yayi nafila yakwanta Yadade yanajuyi kafin barcin yadaukeshi saikusan asuba washe gari sukuku yawuni Sam baida walwala Bayan sunyi break dazasuci abincin rana yahau samanta saiyasamu tana sallah bayan jiya yatambayeta kwana nawa takeyi tace biyar kenan karya takemasa??? Baicekomaiba yace tafito suci abinci"" itakanta jikinta yayi sanyi daganin yanayinsa"" Dadare bayan sunyi saida safe da lubcy sukayi dakinsu wannan karon saida komai yakusa kankama tasomajin amai"" dasauri tasauko tashiga toilet Tanashiga taji batajin komai""" Usman tunyana saran fitowarta haryagaji yaje bakin kofar yana bubbuga mata shiru kuma tasa sakata karshe dole yahakurah yakoma bangarenshi Tundaga ranar dazaran yashigo dakin saitaruga toilet karshedai centake kwana har akakusa kwashe watadaya karshema saiya samata ido Duk halinda sukeciki baisanardà lubcy ba itakuma bata nunawani abuba suna zamansu lfy zaman gaskiya da mutunta juna tadauki yayan Usman kamar nata Zaune suke da marece lubcy tamike zuwa kitchen tazubo lemu a cup biyu tadawo falon tazauna tayiwa suwaiba bisimillah tadauka tasha sukaciga dafirah Dadare bayan Usman yadawo dayake anraba girki yau hannun lubcy yake bayan sunci abinci suntaba firah sukaiwa juna saida safe Aisha✍🏼 ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠ chapter 34 By Gentle Lady💃🏽 Bangarenshi suka nufa tayo wanka shima yayi"" suna kwantawa yakuramata ido"" tasaki murmushi tace akwai matsalane??? Ido yalumashe sannan yabude yace sosai ma tace mekake bukata inyimaka yanzu?? Yace ke kawai nake bukata"" tayi masa kallon rashin fahimta tace haba jiyafa kabaro bangaren kanwata kana nufin haryanzu baka koshiba??? Tonayafe kwanan nawa wlh kakoma cen wajenta Yakalleta da tausayawa aransa yace mace tagari kenan kekina tausayamun bakisan waccen bata tausayinaba "" tadan tabashi tace injidai bawata matsala naga kayi shiru?? Yace hmm bakomai nidai kitaimakamun zatayi magana yadorah lallansa akan bakinta daganan yacigaba da aikamata sakonni jikinsa yanda kukasan Mazari saidai babu yanda zaiyi saidai kawai yayi wasa da itah yadan samu natsuwa kadan Bangaren suwaiba kuwa tunda tashiga daki takasa barci wata muguwar sha awace tataso mata tarasa yanda zatayi takwanta Amman Sam barcin ya gagara daukarta Mikewa tayi cikin sanda tafito waje tafito daga bangarenta tasauka kasa tafita waje"" dakin driver gidan tawuce kaitsaye babu wani tsoro ko shakka acikin zuciyarta Taturah kofar saitajita rufe ahankali tasoma bubbugawa cikin barci yaji anabuga masa kofa yace waye cikin muryan rada tace nice kabude ba lafiya dasauri yazo yabude kofar yana budewa tayi kududuf tashige Dagashi sai gajeren wando takalleshi tundaga sama harkasa tahadiye yawu wani irin shu umin kallo take jifanshi dashi Yana kallon kofa cikin tsoro yace suwaiba meyakawoki dakina??? Murya takaryar tace haba kb yazakace meyakawoni dakinka Harkamanta soyayyarda mukayi dakai??? Tsaki yaja yace soyayyar banza aikinsan inasonki kina sona Amman danbanida kudi akahanani aurenki Kituna shekararmu biyar tare"" sake matsowa tayi kusa dashi tace kayi hakuri masoyina wlh nikaina badason raina akayi auren nanba kaikasan inasonka babanane dayaga kudi yace bazan aurekaba Yace kinga malama banason dadin baki kifita kibarmun daki banaso alhaji yasan wata alaka tataba hadani dake danzan iyah rasa aikina kuma dashi na dogara Tamarairaice fuska haba KB baidace kajuyamun bayaba kayarda dani wlh ina mutuwar sonka Allah yarigada yakaddaro saina auri wannan alhajin Amman wlh banasonsa Yawatsamata wani mugun kallo yace kifita kibarmun daki wlh konaimaki ihu Ninarigada nafiddaki araina tunranarda nasan maigidana kika aurah""" abunda suwaiba takeji bazaisa ta iyah hakurah takomaba"" zanenda yake jikinta tacire tadawo daga itah sai wasu arnayen kayan barciii KB yasoma kallonta tundaga kasa harsama tuni jikinsa yasoma kyarma yadimauce daganin surar jikinta sha awarta ta tasomasa shedan yanata haskomasa ni imarda zaikwasa ajikinta Ganin natsuwa takauce daga gareshi yasa tatako cikin takun Jan hankali tafada jikinsa tasoma kaimasa Sumba tako ina take yasoma maidamata da martani lubcy ce tamike tanarike da kirji tashinta yasaka Usman mikewa yace lafiya??? Tagirgiza kai cikin damuwa tace ba lafiyaba gabana nakejin yana tsananta faduwa Anya antynsu lafiya take! Dayake hakan take kiranta yace kikwanta bakomai bane bakiyi addua ba dazaki kwanta tace nayi Amman haryanzu baidaina faduwaba Tamike nidai barnadubata ganin tamike shima saiyatashi yabiyota harbangaren suwaiba saisuka kofar abude Dasauri taturah tashiga da sallama harkurya basugantaba gabaya suka bade dakunan danema batanan hankalin Usman yatashi dasauri yasauko kasa lubcy tanabiye dashi sukadubà kaf bata gidan yanaturah kofar fita yajita bude kaitsaye yafita dayake dakin kabeer shine farko yayi hanyar dakinsa arude Damamaki yajikofar abude dayaje domin kwankwasawa"" yaturah kofar yanacewa kabeer taso gida ba bakinsa yasankame ganin abunda idanuwansa sukai arba dashi Kalu innalillahi wa inna ilaihir rajiun"" shine abunda kawai yake furtawa take hawaye sukafara sintiri akan fuskarsa Ganin baifitoba lubcy tace alhaji nataada maigadi yace bata fitaba tayi maganar tanashiga dakin ganin abunda yake faruwa lubcy tabuga salati dakarfi salatinta yafargarda KB yadago kansa dasauri Lokacin yana kokarin shigar suwaiba dayake budurwaçe baisamu hanyaba yanashiriñ shigarta dakarfi lubcy tayi salati Wanda yadawodashi duniyar gaskiya aidasauri yasauko yaja zanin gadon yarufe jikinsa saizare ido yake gawani zawo dayaji nantake Muryar suwaiba yaji tanacewa haba masoyina yakadaina abunda zakayi karkaji komai dama jikina nakane kasan kaikawai nakeso" tamiko masa hannu kazo mufaranta ranjunanmu nadade inajiran wannan ranar dazan mallakamakà Kaina Ido rufe take maganar dukda turarta da KB yakeyi dantarufe bakinta ganin bazaitasoba tadago tafada jikinsa tasoma lalaubàr bakinsa Usman daya sandare waje daya tamkar gunkii wani bakincikine yatokareshi gakahon zucii baisan sanda yararumi wayar TV ba yatuzgeta dakarfiii yasoma aunamata itah saukar bulalar dataji ajikintà yasaka takwallah kara Ko kakkautàawa bayayi idonsa yarufe tuni yazulawa KB shima Wanda yasoma kuka ganin abunda yake faruwa ga suwaiba Da itah dashi sukarude gidan tuni ma aikatan gidan sukafito kowayaga abunda kefaruwa saidai yajuya yana tsinemàsu Ganin zai iyah kashesu yasa KB yadauki kayansà ahannu yafita dagudu"" tuni suwaiba tasuma Amman Usman baidaina dukantàba saida lubcy tarike bulalar cikin kuka tace sokake ka kashetañe hàbà tundazu naketa bakahakurii Wani mugun kallo yawatsomàta idanuwañsa sunyi jajir itah kañta tàfirgita dàyana yinda taganshi danbatà taba ganiñsa cikin irin yanayinbà bulalar hannunsa ta rike kam dole yasakarmàtà yàfità dakin dasauri ko kallon masu aikinda suke tsaitsàye baiyiba yayicikiñ gidaa Labila tanafalo saikuka take tana rungume da majeed Dan hayaniyar gidance tatasheta takasa fita saizagàyen falon takeyi gànin dadynta yashigo taruga tafada jikinsà tanakuka tureta yayi yahau sàmañsa Dasauri Aisha✍🏼 ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠ chapter 35 By Gentle Lady💃🏽 Mamaki matuka yacika labila tana tambayar kanta meyasamu dadynta yau"" majeed tuni yakoma barci daman"" Bangaren lubcy kuwa" tana ganin yafita tadauko ruwa dasauri tawatsawa suwaiba take tafarfado tachandara ihu Lubcy tarufe mata baki tace Dan Allah kidaina ihun nan makota sunajinmu fa"" sai alokacin hankalinta yadan dawo jikinta takallijikinta taga batada kaya dasauri tajawo zanen gadon tarufe jikinta dashi tafashe dakuka tana girgiza kanta nashiga uku Yazanyi Anty"" lubcy ce tadafata tace kiyi shiru kinji kanwata tashi mukoma cikin gida "" idanuwanta tadago zuna zubarda kwalla tace Anty na aikata babban kuskure arayuwata wlh aikin shaidanne ninasan idan mahaifina yaji wlh saiya kasheni Lubcy tanisa tace bama zaijiba insha Allah kitashi muje kigasa jikinki gobe zanbashi hakuri"" tasake kallonta akaro nabiyu tace wlh nasan bazaitaba hakura ba kakama matarka da yaronka suna aikata zina ai hankalima nazai daukaba ballantana tunani Lubcy tace hakane Amman meyakaiki aikata hakan da iliminki??? Tashare hawaye tace Anty wlh banason baban majeed wannan shine saurayina atadalilin kudin sa dayace yanasona sai mahaifina yadage saina aureshi nima sainaji inasonsa narabu da kb saboda baida kudin aurena Tunranarda nazo gidan nan sainaji Sam banasonsa soyayyar kb tasake linki acikin zuciyata hardai ranarda naganshi gidan nan amatsayin driver duk hanyarda zanbi dannaga nakadaita dashi bansamuba saiyau da shedan yakadamun gangarsa batareda kokonton komaiba naziyarceshi domin yakawarmun da muguwar sha awarda tatasomun tasake fashewa da kuka tace wlh Anty niba yar iska bace bantaba yin iskanci dakowaba yanzun ma ina mamakin kaina da abunda yakawoni dakinsa nayi takaicin wannan ranar Lubcy tajawota jikinta cikin alamun tausayawa tace na fahimceki Amman mahaifinki baikyauta makiba aiyanzu andaina auren dole kinga saka kayanki mukoma cikin gida Tadago dasauri tana girgiza kai tace wlh zai iyah kasheni tatoshe bakinta saboda kukanda yakwacemata Tace taya zaikasheki kitashi muje kinga masu aikin gidan nan suna waje mujeciki Dan Allah tamike tajuya tace kisa kayan Bakin kofa tafita tasamesu tsaitsaye bata fuska tayi tace tomekuke jirah kowa yakoma yakwanta sumui sumui sukawuce tana tsaye saida takwatanci tasa kayan sannan tashiga taja hannunta suka wuce cikin gidan Cikin falon suka samu labila zaune rungume da majeed tana ganinsu ta ajeshi tace mom lafiya??? Meyasamu Anty??? Me akaiwa babana???? Wadan nan tambayoyin tajefowa lubcy tace bakomai kidaukeshi kukoma daki dagahaka batace komaiba tawuceda suwaiba zuwa dakinta Harkuryar daki takaita ta zaunarda itah fita tayi zuwa kitchen tasamu ruwan zafii tagasamata jikinta tabata magani tace tasamu takwanta Ta share hawaye wadanda suketa zubowa akan idonta tace Anty konakwanta wlh bazan iyah barciba Tace kiyi hakuri kidaina kukan nan saiya haifarmaki daciwon kai kikwanta kinji kaitagyada mata itakuma tamike taimata saida safe hartakai kofa takirata Anty Ta amsa tareda juyowa tace nagode da soyayyarki agareni agaskiya kinchanchanci duk wata soyayya dankuwa samun mai irin halinki sai antona nagode Tasaki lallausan murmushi tace karkidamu yiwa Kaine tawuce tana sakin shu umin murmushi aranta tace kadan kenan yarinya wannan aikin *hatsabibin boka* ne kaitsaye bangarensa tanufa Taturah kofa tajita kulle tayita bugu yayi banza da itah karshe takoma bangarenta takwanta Daga labila har Usman suwaiba babuwanda yaruntsa nasan bangaren KB ma hakanne Amman lubcy barci harda minshari Bata farkaba sai bakwai agurguje tasauya kaya"" koda tafito masu aiki harsungama komai saidai tazuba akula tadaura saman dinner Bangarenshi tanufa taturah kofar saitajita bude da sallama tawuce ciki tsaye tasameshi yanadaura agogon hannunsa tace ina kwana Batareda yakalletaba yace lafiya yadauki takardunsa da key din motar sa yafita"" dasauri tabishi tana kiransa kowaigenta baiyiba harsuka sauko kasa Labila tsaye da itah da majeed sunyi shirin skull cikin uniform Lubcy tasauko kamar tafadi tace abban majeed Dan Allah katsaya Afusace yajuyo yace wai lafiya??? Idan natsayà mezanyimaki"" gabanta saida yafadi tadan dake tace bakomai naga zakafita bakayi break ba Yace nakoshi yasakai yawuce labila""tabishi dasauri zuwa waje tanakiràn sunansa kamar karya tsaya bayaso labila tafuskanci hàlinda yakeciki ya juyo tareda kirkiro da fara a Takaràso tace dady morning"" yace morning my doter kintashi lafiya tace kalau idanuwanta sunakawo kwallah Yace menene nakuka labila" yayi maganar yana dago habarta tace dad nagakamar kanacikin damuwa Dariyar yake yayi yace bakomai banada damuwa maza Kira majeed insaukeku makaranta Tace dad kabeer fa??? Yadanyi Jim sannan yadago yace bayajin dadi yatafi gida maxa kirashi karku makara Tace to sannan tajuya cikin gidan yabita dakallo yacije kasan lebonsa"" Lubcy kuwa tunda yafita tayi tsaye sakeda bakiii suwaiba wacce tasauko duk akan kunnentà komai yafaru dasauri takoma saman tanakuka Aisha✍🏼 ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠ chapter 36 By Gentle Lady💃🏽 Tana shiga batako kalli wajenda mom dinta takeba tadauko jakarsu tariko hannun majeed sukawuce Murya asanyaye tace inakuma zakuje baku karyaba"" batareda tajuyoba tace munkoshi tafita abunta driver n dady ne yatukasu yafara kaisa company sanan yabiya yakai labila yakai majeed shima Lubcy guiwa a sake tahau saman ta takasa tsaye takasa zaune karfa wannan abun yashafeta ranarda aka kawo Amarya aranar tasanarda *hatsabibin boka* bayanin labila da abunda tafada Yace kwantarda hankalinki nasan mezanyi mata"" cikin saurii tace karfa aimata wani abun nacutarwa yatace Yamurmusa yace nasanda haka bakomai zanyimata ba zankullemata bakine koda tayi niyar sanarda wani abunda kikeyi zatakasa magana Kodakuwa akan idonta kikai kisan kai bazata iyah sanarda kowaba tamurmusa yauwa hakan yayi saikuma maganar wannan shegiyar matar wlh boka banason tadade gidan nan Inatsoron karwani Abu yashiga tsakaninsu kasanshifa dashegiyar lakuwa"" yakece da dariya yace abunda naimasu wlh koda dagashi sai itah ne acikin duniyarsu bazaitaba kusan tartaba Yace gobe kiduba cikin drower dakike aje madubinki Zanbada wani magani akawomaki dazaran kinji kina ra ayin tabar gidan kizubamata a lemu abunshadai tasha Toranar zatanemi namiji mukuma zamu turata wajen driver ngidanku Dan tsohon saurayintane idan bakimantaba nafadamaki . Tagyada kai dazaran kinji gabanki yafadi to sunacen tare saikiyi yanda zakiyi kifitardashi harkuje dakinsa Inda za akawo maki maganin zakiga wani Abu cikin kwalba saiki daure bakin kwalbar bayan kin tabbatar tasha maganin daganan komai zaifaru zakigani Godiya tahauyimasa sannan tamaida madubinta"" watan suwaiba biyu yanzu agidan saitazuba mata maganin kuma takulle bakin kwalbar Shine dalilin abunda yafaru tadan nisa akwai matsala watakil nayi kurene gashi laifinta yana nema Nina yashafeni gashi dasafe bahalin kiran *hatsabibin boka* Ranar babuwanda yakarya agidan tana ganin ranatayi takulle bangarenta tadauko akwatin tadauko madubin bayan tagama kiransa saigashi yabayyana tazayyana masa komai Saida yayi dariyarsa wacce yasaba sannan yace laifinkine keda nacewa kidaure bakin kwalba shine kikadaure tamau kisani zuciyarsace kika kulle babu inda iska zaishiga danhaka kuncine yaketa mamayar zuciyarsa Bayajin sanyi kokadan wannan dalilinne bazakiji dadinsaba idanma kika matsa hukuncinda zai yankemata yashafeki Ido tawaro tace nashiga uku to yazanyi yanzu??? Yace abune maisauki kisassauta kamunda kikaimasa shikenan zai sauko Tasaukarda nannauyan ajiyar zuciya nagode boka ahuta lafiya tana miyarda nadubin tadauko abun ta sassauta daurin tamiyar ta aje saiyanzu taji hankalinta yadan kwanta Baidawo da ranaba koda dare baidawo dawuriba"" yanashigowa dakinsa yanufa bangarensa yayi wanka yasaka kayan barci yafeshe jikinsa da turare yasauko zuwa dakin lubcy Kwance takesaman gado abun duniya yashamata kai tunaninta daya karfa reshe yajuyeda mujiya?? Duk da tayarda da boka tasan bazaiyi abunda zai cuyarda itaba Da sallama yashigo dakin Amman batajishiba saman gadon yahau tabayanta yarungumota yasunbaci wuyanta Kamshin turarensa tareda sunbatardà yamata sukadawo da itàh duniyar gaske ahankali yaradamata akunne juyo kikalleni Shiru tayi komotsi batayiba hànñu yasaka yajuyoda itah dakansa Tasanne kanta kasaa hannu yasaka yatallafo fuskarta yace meyasamu gimbiyata???? shiru taimasa haryanzun take yasoma aikamata dayan sako tuntana share shi hartasoma maidamasa martani Sundade suna wasa dajunansu saida yasamu yar natsuwa yasake jawota jikinshi Tadago tana kallonsa idonsà yanarufe kamar maibarci tace baban majeed murya atausashe yace inajinki akwai matsalane??? Tace akan kanwat batagama rufe bakiba yàsà hannu yarufematà bàki yace barci nakeji night Baisake dago kai yakalletaba yajata jikinsa yacigaba dà barcinsa itama ahakan barcii yadauketà . Tundaga ranar baisake haduwa da suwaiba ba itakuma batada aiki saikuka duk tarame saboda tunanin makomarta . Girki yanadawo wà hannuñta lubcy tace tashirya susameshi dàkinsa tabashi hakuri dadare lubabatu dakanta tashirya suwaibà Cikinwàni bugaggen less tanajin dawowarsa tariko hannuntà sukai bangareñshi kirjin suwaiba sàifaduwa yake Lubabatu cegaba taturah kofar da sallama yàña xaune saman kujeràh yana danna laptop lemune ahannunsa yanasha .yadago yakallesu kallodàya yamiyada hankalinsà wajen abunda yakegabansa Aisha✍🏼 ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠ Chapter 37 By Gentle Lady💃🏽 Lubabatu tace barka da hutawa yace yauwa barka batareda ya dagoba"" tadanyi jim sannan tace dama dama wajenka mukazo Yace inajinki to"" tasake gyara zama tace akan kanwata ne Dan Allah kayi hakuri akan abunda yafaru Tayi shiru tanajiran taji mezaice yace yakiikeso ayi yanzu??? Saida gabanta yafadi karfa yace ya yafemata saikuma tadake tace kayi hakuri karkayanke mata hukunci mai tsaurii Sai wannan karon yadago yakallesu suwaiba tunda suka shigo kanta yanakasa saikuka takeyi wani mugun kallo yawatsamata yace munafuka kawai aransa Yamaida kallonsa wajen lubcy yace wane hukunci zanyimata bayan tazabi abunda yazama daidai arayuwarta Saiyanzu taimagana cikin kuka tace Dan Allah Alhaji kayi hkuri wlh bahalina bane wannan shairin shaidanne Baki yatabe yace ban iyah ganewa yace waima menene dalilinda yasaka kika shigomun da itah dakina??? Wlh banason ko kallon fuskarta dazaran naganta raina baci yake Lubabatu tace nasan ranka zaibaci Amman hakuri zakayi tunda babu abunda yafaru tsakaninsu kadaure kahakurah Dan Allah badan halinmuba Yace waikina nufin incigaba da zama da itah??? Hmm abunda bazaitaba yiyuwa bane tunda aka kawo yarinyar nan agidan nan ko hannunta bantaba rikawaba Amman hartayi wayonda zaraje wajen yarona waitabashi kanta tatube agaban wani katon banza suna aikata masha a kuma batsoro aranta batajin tsoron Allah ballantana na mutane tace Dan Allah kayi hakuriii alhaji cikin kuka take maganar Yamike afusace tashi kibarmun dakina banason sake sakaki acikin adanuwana nayi bakincikin aurenki wlh danasan haka halinki yake tunfarko bazan kai kainaba Bata tashiba yasake daka mata tsawa wacce tasakata mikewa dasaurii tajuya lubabatu tace meyasa kakehakan nifa nasanka da hakuri Yajuya mata baya yace banda irin wannan sannan kema ina gargadarki karki sake zuwada itah gurinda nake Tace wannan bahujja bace to akanme"" yace nasaketa itace kalmarda suwaiba taji aidasauri takara wucewa tana kuka Jikin lubabatu yayi sanyi batasake cewa komaiba tajuya tafita abunta farinciki fal ranta amman idan kakalleta zakadauka tanada damuwane sosai kaitsaye bangaren suwaiba tanufa tasamu tanakuka tana hada kayanta "" lubabatu takarasa dasauri tace inakuma zakije suwaiba??? Inazanje bayan inshiga duniya kinsan sarai bazankoma gidan mahaifinaba Dan muddin yaji ansakeni kuma yaji labarin dalilin sakin nawa kashina yabushe Dan wlh zai iyah kasheni"" lubabatu cikin alamun tausayawa tace toki zauna anan mana"" harkisamu miji saikiyi aurenki Tagirgiza kai tace Anty duk yarda kikesona dole kibarni natafi saboda gidan nan"" bawajen zamana bane Lubabatu tace nasani Amman aidarene kibari mana hargari yawaye"" tace bazan kwana agidan nan ba wlh Anty tafiya zanyi Jakarta tadauka tayi gaba lubabatu tabita dasauri tana kiran sunanta Amman takasa tsayawa hartakai bakin kofa sukaji muryansa Yace ina zakije??? Tsaye tayi chak! Batareda tajuyowa tace zanshiga duniyane amsarta saima tabashi dariya Aikuwa yasoma dariya harsuka juyo suna kallonshi cikin mamaki yatsagaita dariyar yace idanma shizakiyi kece kika zabarwa kanki hakan Amman kafin nan dole kizauna kiyi idda adakinki idan kingama idda daganan komai kika yankewa kanki daidaine dagahaka baice komaiba yajuya dakinsa"" Tsaye tayi itah bata fitaba kuma bata komaba saida lubabatu takarbi Jakarta tamiyarda itah Tundaga lokacin suwaiba takoma rayuwar daki saidai idan bayanan lubabatu taje suyita firah yawancin abincima taresukeci Hartayi idda yabata takardar sakinta tareda motarda zatakwashe mata kayanta lubabatu ce tarakata hargida Tabawa babanta hakurii akan karya daketa dantuni dama yasamu labarii makudan kudii tabaiwa suwaiba sukarabu kowa yana kukan rabuwà saidakuma Innar suwaiba takoma rarrashinsu Tace aibasu rabuba tunda mutuncine yahadasu saikusan magrib lubabatu taimasu sallama tawuce Dan gidanma taci abincin dare bayan kwana uku dafaruwan hakan sunayin break dasafe labila tace dady magana nakeso muyi takai karshen maganar tanakallon lubabatu"" Itakuwa saida gabanta yafadi Yamurmusa to yarlele kyabaridai nagama cin abinci tundayau bafita zanyiba kaitagyada masa"" bayan sunkammalà Sukadawo cikin falon sannan yacemata inajinki maganar mezakiyi tanisa tace inaso kasa a kaimu gidan hajiya murmushi yayi yace saboda wannan kawai?? tokushirya zanyiwa Sunday magana yakaiku Tace dady idanfà mukaje badawowa zamuyiba yagyara zamacikin rashin fahimta yace wani Abu mom dinku takemaki Wanda bakyaso??? Tadanyi Jim sannan tagirgiza kanta bakomai dady nidai nafison zama agidan hajiya kabarmu mukomacen islamiyar nan basucika karatu sosaiba cendin zamufi jindadi kuma uncle Hafiz zaikoyamana karatu Yajinjina maganarta sannan yakalli lubcy yace kinji abunda tace menene ra ayinki??? Tace mefa tunda ita tazabarwa kanta kabarta tatafi duk inda zataje mana Amman tabarmun Dana"" tagallàwa labila harara aikuwa majeed yafasheda kuka yace wlh dady nidai wujin Anty nakeso "" yace daina kuka zakabita jikin labilà yalake tasoma bubbugar bayansa cikin lallashi yace tozuwa yaushe zakuje tayi karaf tace harnashirya kayanmu gobe zamutafi yayi murmushi to Allah yakaimu"" hajiya zatayi manyan bakii labila tayi murmushi yace Amman zanyi kewarku tace mumahaka Washegari sukawuce wannan shine mafarin zaman labila kano Aisha✍🏼 ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠ Chapter 38 By Gentle Lady💃🏽 Acen aka sakata islamiyya dakuma boko rayuwarsu sukeyi cikin jindadi dakwanciyar hankali tabbas tasan mamanta ce tayi sanadin mutuwar auren mahaifinta Amman batada halin sanarda wani koda tasofadawa dadynta saita kasa fada"" lubabatu tacigaba da zamanta sai yanda taso gida yakoma nata Saikuma tatsiri yawace yawace kasashe wajen kasuwanci Sam tadaina zama gida babu yanda Usman baiyiba dantadaina taki yace mena rageki dashi mekika nema kikarasa tace bannemi komai narasaba Amman kasuwancin nakeso saboda kawayena duka mazansu sunbarsu suna kasuwancinsu Dayake babanza akabarshiba duk da yanadan cijewa karshe dole yasaka mata ido wasu lokutan tanagida Amman kawai wasa zaiyi da itah Aibashiri yasoma azumie domin gojewa fadawa zina watarana dadare bayan sungama abunda yasaba akullum tajuya daniyar yinbarci Yakira sunanta tadanjuyo tanakallonsa tace yadai??? Nisawa yayi yace waimezaihana muje kasar waje adubaki ni wlh nagaji hakurina yakare ina gudun infada ga hakala Tace toyazamuyi hakurindai xakacigaba dayi" cikin daga murya yace kullum maganarki kenan hakuridai hakuridai shin hakurin haryanzu yabani abunda nakesone??? Sokike garinyin hakuri infada ga aikata zina??? Wlh ninasan Allah yanakareni dayanzu nadade na afkawa ga aikata alfasha Dakudina dakomai "" Amman abunda baifi karfinaba yana nema ya gagareni haba Tace toya kakeso inyimaka inda lafiyata qalau zaka furta hakan to banda lafiya ai Yayi saurin gwaceta yace naji bakida lafiya Amman Allah dayasaukarda cuta saida yasaukarda maganinta Koda banida kudi wlh zan iyah yinrance domin samun lafiyarki Amman inadakudin nan bawai banidasuba Amman kinnace dole sai anan kikeso aimaki aiki Dafarko nayi tunanin kobakyason zuwa wata kasane toyanzu gashi kinazuwa kasuwanci Amman Neman lafiyarkine bazakiba to wlh nagaji kara infadamaki gaskiya nadaina cutarda kaina Tamarairaice fuska tace abban majeed kayi hakuri tomezai hana kayi aure kodan samun abunda kakeso Yace wanne irin aure zanyi agaban idonki komai yafaru nayi auren Amman baikareni dakomaiba saitashin hankali""haba wannan wace irin rayuwace Komawa yayi ya marairaice fuska please lubcy kitaimakeni badan niba dangirman Allah kiyarda aimaki aikin nan Baki tatabe tace nifakoda anyimun aikin Nan bazandauki lakuwarkaba kullum acebawa yanakanyin abudaya kamar abinci haba Wani mugun kallo yawatsamata yace nafuskanceki kenan duk abunda kikemun dagayya kikemunshi ko??? Anya lubabatu kinatsoron Allah?? Mijinki yanason abu amman dantsabar mugunta kihanashi abunda kuma yazama halalinsa ranar gobe kiyama mezaki fadawa mahaliccinki Hannu tadagamasa tace dakata usman shiruna bashine zaibaka lasisin gayamun magana son rankaba "" nihaka Allah yayoni banada jimirin daukar lalurarka danme zakaga laifina tunda banice nayokaina hakanba Zan iya juran komai amman banadaukar bakar magana"" da mamaki yake kallonta Baki budee yace umm lallai yaukinfito mun da ainahin halinki dakika koya wajen kawayenki danni bahakan nasankiiba Kuma Nagode inhar kudi suna biyawa rai bukata kibani sati daya zanbaki mamaki nidakaina bazansake cewa kije ayimaki aikiba Kiyita kumuiniya da kayanki indai jikinkine nadaina rabarsa ballantana abunda kike takama dashii Yatashi daga kan gadon yadaukii kayansa yawuce fuuuu yabarmata dakin"" kallo tabishi dashii ta daura hannu aka tace nashiga ukuna🙆🏿 menene yakeshirin faruwa dani haka""??? Dasauri tadirko daga saman gado tadauki zani tadaura tafito""dakunan dasuke bangarenshi tahau bidaya bayan daya"" kowanne tabuda saitajishi bude Aranta tace kenan bayanan dasauri tasauko zuwa kasa falon kasa tahango haske ta matakala tasauko kasan Chak tatsaya sakamakon abunda kunnuwantà sukajiyo mata"" tasake saurarawa kodai karya kunnuwanta sukejiyomata Yana kwance saman kujerah yadaura kafadaya akan daya alamu sun nuna yanajin dadin firarda yakeyi yalumshe idonsa yace ninedai bawaniba Daya bangaren akace haba ammandai batan hanya kayi nikuma awa daza a kirani cikin wannan lokacin Dariya yayi yace aikinwuce komai awajena kingakuwa kinada mukami azuciyata dannakiraki bawani abubane Tace hakane Amman inakabar uwargidan taka"" bakiyadan mere yace inajin tayi barci nikuma banajin barcii Tasaukarda ajiyar zuciya tace bakaji yanda najiba lokacinda nagakirankà dannituni nafiddarai dasamunka Dariya yasakeyi yace togani nasake dawowa tamurmusa najidadi sosai inasu labila??? Yadan shafo kansa yace suna kano Tace kana nufinwai haryanzu basu dawoba??yace eh yanzu aisunyi shekara acen sukandanzo suganemu tareda hajiya Tajinjina kai Allah yataimaka yace Ameen Aisha✍🏼 ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠ Chapter 39 By Gentle Lady💃🏽 Shirune yabiyo baya nayan dakiku sannan yakirah sunanta samrat tace na am"" yanisa maganafa nakeso muyidake bata wasaba Tadan gyara kwanciyarta tace inajinka yace inaso gobe naturo gidanku maganar aure Baki tarike tace dagaske tareda kalalo ido Yalumshe ido yabude tamkar tana ganinsa wani nishadine yakeji aransa cen kasan makoshi yace dagaske kuma banaso auren nan yawuce sati daya inafatar dai ashirye kike .tarausayarda kai sosaima kuwa"" indai katashi " yace wlh sosai natashi inamatukar bukatarki atare dani Wani mugun dadi taji aranta tace maganina yayi aiki kenan"" dasannu zan mamaye zuciyarka"" yace yanaji kinyi shiru kodai barci kikeji??? Tace barcin lafiya inatare dakai kawai inaganin kamar mafarki nakeyi wainice zaka aurah"" yagyara kwanciyarsa yana fuskantar kasa yace kwarai dama kinsan kamai lokacine yanzun kokacin auren namu yayi bakiji yanda nakejinki arainaba Lubcy wacce saboda tsabar tsurewa batasan sanda fitsarii yasoma bin kafartaba tunda Usman yasoma soyayya da suwaiba baitaba kiranta awayaba Haka zakila baitaba furtamata wata Kalmar soyayya ba waisaigashi yautaji da kunnenta yana fadawa wata kalamai masu sanyaya zuciya Wanda rabon dayazauna yana koramata kalamai masu sanyi tun tana amarya Nikuwa nace kece kiKajawo bakibashi abunda yakesoba taya zaibata lokacinsa wajen fadamaki kalamai bayankuma babu abunda kalaman zasu kareshi dashi Shin mezaihana ke idan bakyada juriyar daukar lalurarsa kibarsa yayi aure mana yasamu wacce zata daukemasa lalurarsa Amman kinhanashi kanki sannan kinhanashi aure kenan sokike yaje ya aikata zina bakyajin tsoron cutar zamanine??? Idan ma baikwaso maki cutaba wlh kincutardashi kinkuma zalunceshi saikisan amsarda zaki kare kanki ranar gobe kiyama agàbàñ mahaliççinmu Dayawa akwai mata masu irin wannan halin musamman matanmu nayanzu inhar bazan baka farincikiba bazan hanaka aureba Watafa tahanashi hakkinsa idankuma yace zaikara aure tace ba aimata adalciba"" aikoda yayi auren bazaiyi adalciba dan Allah jama a kunga laifinsa??? Wlh konine shi inda nakesamun kulawa nan zanmaida shekata kuma komai tanema zanyimata tunda nima tanabani abunda nakeso Daga hakan saikuma tafara surutu tace anmaganceshi gashinan yanabin ta kamar bantee Kullum yana manneda itah kamar jela dasafe bayafita aiki dawuri dadare kuma saiyadawo dawuri Amman bayahaka ranar girkina "" shinwai intambayeki wayajawo hakan??? Kome kikagani kece kikajawo kuma wlh dole kiga banbanciii Kedakanki kinsan dole asamu banbanciii Inakirah ga iyayena yayuna abokaina kannena mata muji tsoron Allah musan yanda zamutafida lalurar mazajenmu mukuma ji tsoron Allah musani komai mukayi sai antambayemu yazamanmu na aure gobe kiyama karmu manta da kwancin kabari tsallakar siradii sannan kuma karmu manta gida biyune alahirah akwai wuta akwai aljanna dole kasamu kanka adaya Allah yasamuna cikin tawagar yan aljanna Ameen Allah yasamufi karfin zukatanmu Gabadaya hankalin lubcy yagama tashi jinyanda Usman yake furtawa wata Kalmar soba itaba wani wawan zagi tafurzar Wanda nikaina bansan ta iyashiba Dasaurii tayunkura domin komawa aranta tana ayyana bamazata bari wannan tashigo gidan ba"" santsin tayes dakuma sanyin fitsarinda tasaki suka kwasheta tafadii jikake kuuuu Tasaki wata kara wacce taisanadin dawoda hankalin Usman saman aikuwa dama bakin bene take hakan akafara gangaroda itah kamar kwallon magwaro sai ihu take tana kawowa kasa tabuga kanta dakarfe take tasuma kantaa yasoma fitarda jini daidai kawowar usman wajen Sam baijiwani damuwa Aransaba kodan tabata masa raine oho"" atsanake yafita yakirah driver dakyar ya iya Kaita mota akawuce da itah hospital Taji mugun rauni akai akayimatà gyara takuma goce akafa"akasamata Karin ruwa"" washe gari akagyara mata kafar Usman yasanardà doctor idan dahali suwuce ayimata aiki kasar waje"" yace aikin mene ai matarka batada wata matsala . Yadubeshi darashin fahimta yace bakagane menake nufiba kwanaki sunsamu hatsarine akan hanya towajen gyaranne doctor yace tanada kari agabanta shine dalilindà yasaka takasa haihuwa dakanta Yabata wadansu magani yace tayi amfani dasu kafin aimata aiki" doctor yayi murmushi yace tanada kari agabanta kuma harka kusanceta tasamu ciki??? . Inhar agabanta yake bazaka iyah kusan tartaba Usman shiru yayi dankansa yadaure"" doctor yalura dahakan yace barinasa akoremaka kokonto Nanyakirah wata nurse yace takiramasà doctor Asma.u tace to tafità babu jimawa sukadawo tare yayimata bayaniñ komai itama yanda doctor yafada hakan tafada Yajuya wajen Usman yace kadaijiko"" yasake kallonta yace kije rum 11 kiduba mana saikizo kimana bayani tace okay tareda fita Doctor yacigaba da rubuce rubucen shi Usman kuwa saisake sake yakeyi aransa yanata jinjina maganar doctor Aisha✍🏼 Copied By HAYATU BABA ZUBAIRU (admin Arewa hausa novels Novels villa Duniyan novels Hayat hausa novels Hausa novels and fashion And Cool novel, makeup and cooking) WHATSAPP NO: +2347039625239 ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠ Chapter 40 By Gentle Lady💃🏽 Bayan kamar mintuna talatin tadawo taturo kofar tareda sallama"" Usman yana ganinta yadago kansa"" kujerar kusa dashi taja tazauna Tanafuskantar doctor Wanda shima ya aje alkalamin hannunsa yana saurarenta tace nadubata batada wata matsala"" Doctor yace shikenan kina iyah tafiya"" tace to tareda mikewa tafita" doctor yanisa yana kallonsa yace dama ninasan babu wannan ajikinta kamanta a hospital din nan tayi haihuwa biyu inda munga wannan matsalar aidatuni mun maganceta Kodama tanada wannan karin ai a take zamucireshi basai andau wani dogon lokaciba haihuwa dabata iyah yidakanta yadanganta dayanayin jikinta sannan kuma yaranta sunada matukar girma kofar jikinta bazata ishesu fitaba Idan munga kamar za arasa wani acikinsu shiyasa harmuke mata aiki"" yakai karshen maganar yana kallonsa Usman yanisa yace nagamsu da bayaninka Amman meyasa doctor yasanardani hakan??? Yace wacce asiviti kenan??? Usman yace abuja"" doctor yanisa yace baxaicemaka hakanba inhar ba ita tace yasanarda kaiba ai itah tanajin yanayi ajikinta koda yafurta zata iyah karyatawa Usman yadago da alamun damuwa afuskarsa yace meyasato zatamun haka??? Doctor yace to wannan amsar abakinta zakajita kabari idan tasamu sauki kuka koma gida saikaji abakinta akwaidai manufaryin hakan Yanisa shikenan doctor nagode bari Nayi waya yabashi hannu suka gaisa sannan yafito hajiya yafara Kira yasanarda itah sannan gidansu lubcy din Ranar hospital din yawuni sai marece su hajiya sukazo labila kinzuwa tayi waisunada harda islamiyya washe gari yangidansu lubabatu sukazo harda kanwar mamanta anan suka barta suka koma Hajiya kwananta daya takoma washe gari aka kai kudin auren Usman gidansu samira mahaifin abdul tareda abokansa sune suka nema masa auren ko hajiya baisanar mawaba danyasan zatace yabari sai matarsa taji sauki shikuma yanason bata mamakine Ranar litinin aka kai sadaki akasa bikin sati daya duk da bahakan Usman yasoba Amman sunce sunason yin shirye shiryene Sai anasaura kwana biyu daurin auren yasanarda hajiya itadai fatan alkhairi kawai tayimasa"" labila dataji labari murna tahauyi harsaida hajiya tabuge ta tace waikinji abunda akafada kiketa faman tikar rawa?? Tace najimana hajiya ba dad ne zaiyi aureba??? To idan banji dadiba mekikeso nayi??? Sainafadawa sahiba muhada faty na musamman .hajiya takaimata duka taruga tana dariya tace banda shashanci mahaifiyarki tana gadon asiviti harta faty kikeyi?? To naga yanda zakihada Fatyn labila tayi cikin daki tana dariya tace aikuwa zakigani"" tunda lubcy tafarfado tamatsa akaita gida batason zaman asiviti Doctor yakibata sallama yace takara hakuri hartaji sauki"" saida kanwar mamanta ta rarrasheta akan takara hakuri Usman yanazuwa Amman bainuna mata yasan komaiba saiyayima kamar babu abunda yashiga tsakaninsu . Wata zuciya tana rayamata kodai yafasa aurenne watakuma tana karyata hakan dole tanason taga *hatsabibin boka* totaya gata agadon asiviti wazatace yadaukomata madubin Takaicii yabi yadameta nan take jininta yahau saida akaimata allurar barci dantasamu natsuwa Washe gari kuwa da azahar akadaura auren samira da Usman akan sadaki dubu Dari hudu lakadan Ranar samira tamkar tazuba ruwa akasa tasha saboda murna"" wai itace matar Usman" mutumenda yace bazai auretaba hmm gaskiya dolene tagodewa aminiyarta datakaita gun bokanta Gashi tasamu soyayyarsa acikin ruwan sanyi yanzu dazaran tashiga gidan saikuma tayi yakin fitarda kidahumar matarsa wani murmushin mugunta tasakii Saina rabaka da itah yazamana bakowacce mace agabanka faceni tasakeyin murmushin jindadi Da marece motocin kai Amarya suka dauko samrat zuwa gidan Usman ranar ko asibiti baikomaba tunda yaje dasafe Ranar Usman kam yahuce takaici dankuwa samrat batahanashi kantaba saida yabarshi Dan kanshi koshima yatausaya matane ganin tawahala sosai Bayan yayi wanka yayi sallah yanamai godiya ga Allah daya sharemasa hawayensa yabashi samrat Lubabatu tana asiviti batasan wainarda ake toyawaba"" yakanje dasafe kuma yajemata da abinci sambata kawo yayi aurenba Amman tagayanzu kullum cikin fara a yake kamar tatambaya saidaikuma takama bakinta Kachar tabari takara sati tamatsa dole aka sallameta ta tattara takoma gida ranar kanwar mamanta tatafi Tunda Usman yafita baidawoba saidare"" lubabatu tana bangarenta kaitsaye bangarensa yanufa yayi wanka sannan yatafi bangaren samrat Cikin falonta yasameta tachanchade cikin adonta tayi kyau tana ganinshi tamike tatarboshi kiss yamata akumatu yace Amarya Kinsha kamshi Tayi farida ido tace andawo lafiya"" yace qalau dauko mayafinki muje bangaren maman majeed kidubata tace to tareda wucewa tadauko sannan tafito suka jerah sunayar firarsu ta ma aurata Tunda lubabatu taji muryan mace gabanta yayanke yafadiii" shine gaba tanabayansa yaturah kofa da sallama lubabatu ta amsa fuskanta tanakan matar da sukashigo tare Usman ne yanuna mata waje yace tazauna kusa dashi tazauna tareda gaidata Anty inawuni yajiki Duk daharyanzu lubabatu takasa yarda dagaske usman aure yayi tanakan gadon asiviti tace qalau naji saukii yagidan Tace Alhamdulillah "" usman ne yace maman majeed ga zainab amaryatace yajuya wajenda zainab take yace zainab ga matata kuma farincikina itace ni nine itah inasonta fiye dakomai banason abunda zaibata mata rai inafatar zakitayani wajen faranta mata rayuwaa Baki tatabe cikin ranta tace basaika fadamun yanda kakeson matarkàba jinhakan bazaihana inrabakuba Amman afili murmushi tasaki tace karkadamu zanyima fiyedakai murmushi yayi yace nagode yajuya wajen lubabatu yace ga kanwakinan dan Allah inhar tayi badaidaiba kitsawatarmata kiyita hakuri kuma dukda nibanida matsala ta bangarenki Tasaki murmushin yake tace karkadamu bazantaba sauyawa ayanda kasanniba fatanadai Kanwata tarikeka amana""" takai karshen maganar tanajifartà dawani kallo nikam nace dàbiyu kenan Kusa dàkunnenta yaradamatà magana kigodewa kanwarnan taki tanaji dani sosai nasamu abunda nakeso gaban lubcy yabada rass tace nashiga uku😳 ya akài hakan tafaru????gabadaya tashiga tashin hankali Amman dayake yarduniyace saita wayance Aisha✍🏼 ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠ Chapter 41 By Gentle Lady💃🏽 Tace kai Amman naji dadi sosai hakan nakeson ji """ Allah yabarmun Kanwata"" yace ameeen itakuma samrat kunya duk takamata tamkar tanutse agurin Fuskarta yashafo yace to yamaganar raba kwana tunda yanzu hartayi sati daya"" rausayarda kai tayi tace kaga banada lafiya haryanzu dasaura Kawai kabari sai nanda satiii biyu kafin nan nawarke kaikuma kaci amarcinka sosai"" wani dadine yakamshi baisan sanda ya makaletaba yasakar mata kyakkyawar sunba abakinta Wani mugun kishi yaturnuke samrat kamar tasaki kuka"" lubcy talurah dahakan"" cikin ranta tace ke kenan dakika tsinceshi darana tsaka inakuma gani da nayi shekara shabiyar tare dashi"" mekiike tunanin zanjiii Afili kuwa saita dantureshi " murya kasa kasa yace please kibarni naji dimin jikinki Sam shiya manta yana tareda samrat lubcy ce tace baban majeed Kanwata kaifa takejirah naga alama kamar barci takeji Sai alokacin hankalinshi yadawo jikinsa wata uwar kunyace takamashi yadan Sosa kai sannan yamike yace mujeko samrat"" mikewa tayi tadan kirkiro murmushi tace Anty saida safe Allah yasauwake Tace ameeen Amarya nagode saida safe gaba tayi abunta yana bayanta harsuka bude kofa tafita shikuma yadawo dasaurii yasunbaci lubcy abakinta nadan tsayin lokaci sannan yadago yalunshe idonsa yabude fuskarta yashafo yana kallon cikin kwayar idonta kamar mai karantar wani Abu . Tace kabarta tsayefa"" murmushi yasaki sannan yace saida safe yawuce koda yafita samrat bata wajen dasauri yabi bayanta"" bangarenta yasameta Kuka take Amman tanajin motsinsa tagoge hawayenta tasake gyara fuskarta saman gado tahau dasauri tarufe jikinta" da bargo Yanashigo wa yayi sallama ciki ciki ta amsa masa sallama saman gadon yahaye yadaga bargon yashige ciki"" idanuwanta arufe suke fuskarta bayabo ba fallasa Ido yakuramata daga bisani yace yahaka kuma samrat??/ tace damefa??? Batareda tabuda idontaba yace hmm yau bazamuyi firabane??? Tadan muskuta nibarci nakeji"" Yace tofa wannan shan kanshin wai duk Na menene?? Baki tatabe tace barci nakeji kawai"" yace kuma nibazan barki kiyi barcin ba chakulkuli yasoma yimata Tasoma kyalkyatar dariya tanacewa bataso yabari"" yace shikenan barikawai inkoma wajen antynki dama dantanason kibani kulawane tabarmana kwananta Yayi maganar yana yunkurawa daniyar tashi hannutasa tajawoshi yafada jikinta take sukasaka dariya subiyun yace af ashedai anasona ba ason nadaga Taharareshi cikin sigar wasa tace zanrama wlh dariya yasoma yimata takaimasa dukan wasa hannun yarike suka soma kokawa daganan suka zarce wasa yasauya Bangaren lubcy kuwa sunafita tatashi da dingishi tarufe bangarenta tawuce kuryan dakinta tadauko madubin tashafa tareda kiran sunan *hatsabibin boka* Cikin second daya yabayyana acikin madubin yanayinda lubcy takeciki kallodaya zakaimata kagano tanacikin Matsala . Kafimma yayi magana tafashemasa dakuka""" kukanda yasaka shikuma yasoma sheka wata irin dariya saida tagaji dakukan tatsaya sannan yace mata menene dalilin kukanki Tadago raunannun idanuwanta tace inaso akashe wannan matar mutuwa mafi muni waitayama taci nasaran shigowa gidan nan harta rushemun duk shirina Yace tayanda kikazo masa kisani wannan matar tabanbanta dawadancen"" cikin tsoro murya na karkarwa tace kamarya boka??? Yace saboda itama tanada wani masha hurin boka agunsa tasamu damar ketawa zuciyar mijinki tadusashe haskenki agunshi wannan yasamo sanadi nahanashi kanki dakikai Dama anan akeso kusamu sabani daganan komai zaifara lokacinda kikafadi aljanine yatureki harkikaita gangara zuwa kasa Bokan yayi hakane domin karkisamu damar sanardani indau matakiii"" tace tomeyasa baka dakatar dashiba""" kaiyagirgiza yace niban isah inhana wani abunda sukaimaki yasameki ba yanzu haka Suna shirye shiryen yanda za afitardake kokuma ahaukataki Baki tadafe tace nashiga uku toyanzu yazanyi???boka??? Yakece dawata dariya yace karkidamu aikogaba da gabanta zannuna masu babu maijadani yakwana lafiya Sannan kisani mijinki yagano lafiya qalau kike saikisan yanda zaki kare kanki idan yatambayeki"" domin ta nanne sukasamu damar karya shihirindà mukai makiii Dabaki hanashi kankiba dahakan baifaruba"" tashare hawaye tace nibansan abun yakai hakaba nibanason atausayà Mata tundahar tsautsayi yakaita takwanta damijina totajawa kanta mutuwa Banaso abarta darayuwa"" *hatsabibin boka* yasake barkewa da dariya yace angama kisake yimun magana zuwajibi komenene zakiji bayanie yanzuñ inatsakà dayinwàni aikine nabarkiii lafiyàa Yanakaiwa nan hasken yafito takeyabace lubabatu tamiyardà madubiñ tasoma zagayen falon hankalinta atashe yaukam tasan koda kwanciya tayi barciii bazai dauketaba Aisha✍🏼 ☠ *HATSABIBIN BOKA!!!*☠ chapter 42 By Gentle Lady💃🏽 Taciji dan yatsanta yanzu kenan tashigo gidana tasameni da mijina Amman kuma takeso takoreni?? Hauka kuma to wlh nibazanyi haukaba saidai uwarta tayi Yanda nakeganinta shiru shiru ashedai munafukace"" tanawani cemun Anty Ashe tasan tuggunda tahadamun nimadai nace taya Usman zaiyi soyayya aisaidai yayi aure domin kore sha awa Amman bazaisake sonwata halitta aduniya sama daniba Kema kijirah nakusan fatattakarki daga harabar zuciyarsa bazanyi wasaba ko auren ma bazan barshi yasake yiba ballantana yasamu yanda yakeso Lallai zancen duniya gaskiya duk abunka akwai irinka dubu aduniya Yanda lubabatu tagadare haka taga safiya ko gyangyadi batayiba dasafe bayan yagama break yayi shirin zuwa aiki harsaida suka kawo kofar fita yatuna da lubcy yace wash tareda dafe kansa yajuya dasauri tatari gabansa tace mekamanta kabari indaukomaka Yace wlh namanta bandubo maman majeed ba kinsan batada lafiya" tadan marairaice fuska tace to aiyanzu ka makara kabari saikadawo Mana. Murmushi yasakar mata yace nagode dakulawa Amman kinmanta company nane kuma nine shugaba koda kinzuwa nayi hakan bazai samarda hayaniyaba Tace hakane Amman"" shiru tayi tanajin faduwar gaba Amman dole tadake dantagwada ko maganin jiya yafara aiki tace nidai katafi muje"" sake kallonta yayi cikin murmushi yace nipa bance kirakaniba naga alama kamar hawanne bakyasonyi Kizauna nan nizanje indawo tace bazakaba Allah da mamaki yakalleta yace waike mekike nufine??? Barifa ganin ina lallabaki kidauka banason matata karfa kimanta inada Yaya biyu da itah Kodama banasonta albarkacin yayanda suke tsakaninmu zankula da itah ballana inason matata Idan ma dawasa kike banason irin wannan wasar inkuwa da gaskene kiyi saurin fatattakar wannan tunanin azuciyarki yawuce abunshi Jiki sanyaye tabi bayanshi gabanta yana dukan uku uku tabbas boka yace inhar tasaka abunnan agabanta harya kusanceta to duk abunda takeso dazaran tafurtashi Usman zaizama maibi yayya agareshi Shima zaiso abun ufiyeda itah Amman jiya jiya Abu haryaso fara aiki yanzun kuma yaki anya banyi kuskure wajen saka abunba??? Kai ina daidai nayishi tanadai iyah yiyuwa ko akwai wata matsalane dole na gaggauta kiran raliya tunkafin wankin hula yakaiga kaini dare Dawannan tunanin takarasa bangaren lubabatu kusanma tare sukashiga lubabatu tanafalo kwance saman kujerah tadafe kanta sakamakon ciwonda yakemata narashin barcinda batasamu tayiba adaren jiya Dasauri yakarasa saman kujerar yadagota yana tambayar lafiya""??? Karamin tsaki taja tace wlh kainaciwo yakemun kamar yarabe gida biyu Samrat tadan harareta aranta tace munafukar banza yataba goshinta zafiii rau yayi saurin dauke hannunsa yace haba meyasa zakimun haka bakida lafiya Amman kikasa sanardani Tayi yake tace karkadamu basosai nakejinsaba banaso nadamekune shiyasa fuskarsa duk tasaukarda alamun rashin jindadi Samrat tamere baki saikuma tace inakwana Anty lubabatu ta amsa dasakin fuska tace ya amarci Cikin yanga tace munakancinsa amsar tabaiwa Usman haushi ganin yanda take magana cikin gadara Guntun tsaki yaja yace samomun ruwa kamar bazata amsaba saikuma tawuce kandai kandai kamar yartsana"" Hartafita dakin yasakejan dogon tsaki"" alamu sunnuna ambashi haushi kenan""" yamaida kallonsa wajen lubabatu yashafi fuskarta da murmushi yace kiyi hakuri kinjii Talumshe idonta tabude saboda zafinda zuciyarta takeyi tace bakomai nifa ba aimun komaiba karma kadamu dawannan Janta yayi jikinsa yana saukarda ajiyar zuciya"" tayi lamo ajikinsa ahankali tace dadyn majeed dan Allah kayi hakuri akan abunda naimaka Saitafasheda kuka dasauri yadago kanta yace mekikamun kuma???? Tace ninasan mailaifice awajenka tadanyi Jim abunda naimaka ranar Nafitone daniyar inbaka hakurii sainazame nafadi ranarnaso sanardakai lafiyata qalau dama nayihakane waidan karnasake samun ciki ganin yanda nake wahala waini anawa wautar hakan dabarace Saigashi najawa kaina nasan yanzu bakasona ma" tunda kasamu wacce takebaka abunda kakeso "" ninajima natsani kaina Allah yasama inmut saurin rufemata baki yayi yace yakike wannan maganar Nibanrikeki dakomaiba kuma nayarda da maganarki Amman dakinfadamuñ aisai murika shan magani duk da inason kihaifamun yara dayawa Tace Kayi hakurii bankyauta makaba"" yace bakomai indai tabangarena babu abunda zansamu agurin wata dazaisa nadaina sonkii Tasaki murmushi nagode Allah yabarmuñ kai yace ameeen yasunbaceta saitin bakintaa daidai shigowar samrat wacce takelabe tanajiñ duk abunda sukefadà Shigowarta baihanashi cigaba da sunbatar lubcy ba"" hartakawo wajensu tadauke kantaa gefedaya Tamika mashi ruwan Sam hankalinshi bayagun"" Saida taga yanashirin wuce gonada iri tajaye bakinta hakan baimashi dadiba danyasamu natsuwa Duk indayaje bayajin natsuwa matukar batareda lubcy ba"" saiyanzu yaga samràt yace au ashekin kawo ruwan??? Yayi maganar yanakarbà sorry nabarki tsayeko Ko alamar jinkunyar abunda yayi baiyiba takaicine yakama samrat dayake macece wacce bata iyah siyasaba sannan kuma tanada kishi sosai sambata iyah boye kishinta kokadan Tsaki taja tawuce fuuuu tanakàiwa bakin kofa kuka yakwacematà tabude kofa tafita dagudu Usman yatabe bakinsa tareda daga kafadà alamar baidamuba Karamin towel yadauko yanatsomà ruwan yanadanna mata jikinta tace kanagani tafita tanakukafa!!! Cikin nunarashiñ damuwa yace tomezanyimata tunda badukantà nayiba"" zatayi magana yadorah yatsanshi akan labbantà yace bakida lafiya kidaina yawan magana yacigaba da abunda yàkeyi ahankali zàfiñkan yaraguuu Idanuwañta suna lumshe tace katashi kabita dan Allah yayi murmushi yace waike meyasà kikacika damuwa dawanda baidamu dakeba???? Tabude idonta tace saboda matarkace kumani komai kakeso nima inasoñsa""" cikin tausayawa dakuma soyayya yashafo fuskartà yace wai anya za asamu irinki aduniya??? Kallifa kigani tsakitamun saboda inakulàda matata tanagani kuma bakida lafiya kefa harkwananki kika barmataa Amman waihartake kishiñki kebakiji haushintàba datari kemaki miji tsayin satii biyu Aràntà tace nikuwa naji haushi bana nunawane kawai afili murmushi tayi tace aini natsufa nabarma yara aikishi bashine so ba abunda akekiràh so kasoduk abunda masoyiñkà yakeso Aisha✍🏼 ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠ Chapter 44 By Gentle Lady💃🏽 bayau nasaba fadamaki hakanba kamar inakara cewa kicigaba tashare hawaye tace toyakikeso inyi. . Nikaina bansan sanda raina yakebaciba bana iyah juran ganin wani tareda abunda nakeso musamman Usman danban hadashi dakowaba Raliya tace hu um abunnaki babbane tonidai yanzun mama ta aikeni idan nadawo zanbiya saina sanarda ummar hakan yayimaki??? Tayisaurin gyada kai tace yayi Amman Dan Allah kicemata taje yauyau din nan danni banaso narasa mijina tace karkidamu zansanarda itah idankuma yakasa sainasake karbomaki inda mukaje Tace shikenan sukai sallama tana aje wayar taji tashin motarsa ta window taleka tana kallonshi watakan saiyanzu yaga damar fita takai kallonta kan agogo shabiyu saurah tayi kyacci aisaina rabaku bazan dauki wannan ba Cendinma da akafitardani tafi karfina Amman wannan daganinta sokuwace cikin sauki zanfitarda itah dawan nan tunanin takoma takwanta Bayan kwana biyu dafaruwar hakan lubcy tasake kiran *hatsabibin boka* bayan yabayyana tace maganarmu taranar wlh boka nakasa samun sukuni kokadan inaganin kamar takusa rabani damijina"" Dariya yafashe da itah wacce taisanadin girgizawar madubin saida yadade yana dariyar sannan yagintse fuska yace"wayafadamaki akwai bokanda ya isah yayi jayayya dani Yasake shekewa da dariya sannan yadauko wani madubin yashafa yayi yansurutunsa saigawata wuta tayi tartso saiga bokan ya bayyana acikin madubin daure cikin sarkaa Yanacikin mawuyacin hali yanuna mata"" yace kinganshinan yana ajiye acikin kurkukuna nakarkashin kasa"" babu wani mahalukinda yataba shiga ciki faceni Sannan kuma duk Wanda nasaka aciki bazai fitoda raiba saida najamasa kunne akan kodatazo karyasake yamata aiki Amman saiyayi jayayya nikuma Na aika dakarun aljanuna suka daukomun shi"" yanakaiwa nan yashafa madubin bokan yabace "" yamaida kallonsa"" wajenta yace naturah daya dagacikin aljanuna yayi shigar bokan domin nasamu labarin sunakan zuwa wajensa yabasu magani akan mijinki yadaina kulaki karshema saiya koreki Yanisa dalilinda yasa mukai hakan zanturah aljani hayyanul zairi domin ya magance matsalar Tagyara zamanta tace kamarya boka??? Hannunsa yadaga yasoma kiran hayyanul zairii saigawani haske yabayyana kafin kyaftawar ido saigawani kyakkyawan aljani Yabayyana ciikin shigar bil Adama kamarshi sak Usman lubcy tazaburah bakinta yanarawa tace wannan ai mijinane *hatsabibin boka* yasake kecewa da dariya yace wannan dakikegani bamutum bane aljanine shine Wanda zaigama maki aikinki cikin saukiii Lubcy tayi tsuru kamar tasaki fitsariii yacigaba zanturashi wajen kishiyarki azuwan mijinkune"" cikin rashin fahimta tace to ainikuma bazan banbance tsakaninsuba karfa asamu sabani Yasake shekewa da dariya yace awajenki fuskar bokanta zakigani cikin kyakkyawar shiga mijinkima haka sauran mutanema haka Amman awajenta zataganshi mijinki kullum zairika zuwa yanadaukarta sunafita unguwa kowasaiyasan dahakan ranarda mijinki zaiganta aranar aljanin zaikasheta yashanye jininta tareda bokanta saiya sawa motar wuta Kowa zaidauka hadarine sukasamu sannan kowabazai zargekiba itakuma zatadauka aikintane yaci yayi shiru yana kallonta Sannan yace dangane damijinki kuwa tunda dakinta yake kwana zamuhada maki wani maganie gobe gobe kibabbatar tashashi Dazaran sunkebe adaki zatarika sakin wata irintusa maishegen doyi"" idankumà takwanta kafinsafe zatayita fitsariii .nasan mijinki babu abunda yatsana kamar kazantaa cikin kwana biyar zamumaidatà kàzama Mijinki bazaisake shiga dakinba daganan hayyanul zairi zaifara aikinsaa Amman kafin nan sunce kituromàsu kayan aikii Zakiga abunda kikeso"" tawashe hakorah tace gobe gobe zakagansu godiya nake daganan yabace tamiyarda madubinta Washe garikuwa tacewa Usman tanason zuwa gidansu sajida tadubata batada lafiya "" sosai yasotabari yakaita tace ah ah aitasamu saukii zataje dakanta Yabata kudiii masuyawa tàyiwa sajida sayyyar kayàn jinya kaitsaye kasuwa tanufa tasiye dabbobin Shannan tabiya gidan sajida sukasha firah ice cream tasiyo tazo dashi gidan ta ajeshi yahuce saida taga maganin tabarbada tabarbada aciki tayamutse tasaka cikin fridge yayi kankarà Dama sunadàn tabafirah akasa kafin yadawo tasaukomasu dashi"tabata daya tasoma shannata""" itama tafara shaa Tace kaigaskiya akwài dadi Anty idandawañi kikaromàn"" tace ashedai kinasonsa sosai bari nàdàukomaki Aisha✍🏼 ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠ chapter 43 By Gentle Lady💃🏽 Yace Amman bakowacce mace tasan wannan ba ko??? Dankuwa dakowa yasani aida samrat kwata kwata bazatayi kishinkiba Kodayake hali badayaba"" tamurmusa tace lokacintane taci yarintarta "" murmushi yayi yace yarinta da kishi aibazaiyiba yamike yadauko mata maganin ciwon kai yasauka kasa yahadamata tea tasha sannan yace sukoma cikin daki Tace aikifa zakaje"" murmushi yasakar mata yace karkidamu dakinsamu barci zantafii yayi maganar yanajan hannunta suka shiga dakinta . Yakwantarda itah yanashafa bayanta ahankali"" cikin yan mintuna kalilan barci yashureta damakuwa barcin takeji Bangaren samrat kuwa tanafita tayi bangarenta tanata darzar kuka"" abunda yake kasa gareta takwakwaloshi tayar tana hara rarsa tamkar shine yayimata laifi Lallai tsuguno baikareba tana takamar tashigo gidan Usman asaukake ashebatayi komaiba yanda take tunanin yanason matarsa abunhar yazarta tunaninta Wayarta tadauko takamo lanbar raliya tasoma kirah"" saida takatse tasake Kira sannan tadaga tafashemata da kuka Cikin tashin hankali tace raliya inacikin matsala Dan Allah kije kifadawa mamana wlh aikin nan data bani baiyiba Raliya tace bangane baiyiba wajenwa ta karbomaki maganin??? Tashare hawayenta tace wajen bokanta nima dai bansanshiba kuma wlh nayi duk yanda tace Raliya tanisa tace tomenene nakuka kuma?? Kodai kinyi halin nakine nasanki dashegen kishin tsiya Tashare majina tace haba raliya kinsan meyamun kuwa???? Tace inakuwa zansani basaikin fadamunba "" anan takwashe komai tasanarda itah Tace haba aiko zuciyar dutsece dani dole inji haushi agabanafa yahau tsutsar bakinta kamar yasamu mintiii Raliya tafashe da dariya hartana rike ciki abun yatunzurah samrat saitasake fashewa dakuka tace yanzun sakayyar dazakimun kenan duk irin abunda naimaki nikuma infadi bukatata kihauni da dariyar mahaukata bakomai nagode sai anjima Tace please karki katse wlh badariyar mugunta nakemakiba ina mamakine kisamu mace damijinta harda yaranta Amman kifita kishi Tace to aikishi halittace kikasani ko itah ba ahalicceta dakishinba""" tayi maganar tana harare harare kamar raliyar tanakusa da itah Raliya tace kowacce mace dakikagani tanada kishi akan abunda take so damadai batasonshine zakifadi hakan . Amman kinsan tanasonsa tundahar tahaihu dashi kawaidai kishin watane yafinawata kuma bawai finshi yayibaa kawaidai akwai masu boyenasune Wannan shine babbar matsalata dake rashin boye kishinki menene yakashe maki aure dafari bawannan mahaukacin kishin nakiba Kisani komai maganinda kikeyi"" muddin kinada kishi sosai maganinki bazaiciba"" kishi yanarage karfin soyayya azuciyar miji Bawaikuma kinuna bakya kishinba yasan kinayi Amman saikidanne kiga yanda matarsa tayi kincefa tana asiviti akayi aurenku Amman datadawo maimakon tatada fitina saimatace tayafemaku kwananta Tabaku harsati biyu kusha amarci atunaninki tagaji damijinne??? Kodaya kawaidai tasan komai narayuwar tafiyada danamiji Anan zandanyi magana akan mata masu shegen kishin tsiya watakishin nata kamar badiyar musulmaiba Kisani kishi mafarin sakine domin duk macenda tafaye kishi dawuya kaga aurenta yarane ba asaketaba "" nikaina matanda nasan ansaka gameda mugun kishi bansan iyakarsuba To kintada bakin kishinki adole kekawai zakizauna damiji kuma anfisamun haka awajen uwargida tunkinayi mijin yana lallabaki karshema yabuge iskanki Ninasan wata wlh tanatare damijinta baida arxiki sunatare haryayi kudii lookacinda yadace tazauna taci arziki akan yakara aure kishi yaturata tahau bala I taki kwantarda hankalinta Tundayayi aure baida kwanciyar hankali kullum cikin fadatake da amaryar tunyana lallashiñtà haryagaji yagano itace batason za man lafiya Zancenda nakemaku yanzu wlh yasaketa saki daidai har uku dadaya daya akafara koda yasaketan takoma gida idan aka sulhunta tadawo maimakon tagyara hali saitadorah daga inda akatsaya Abunda saki yakenuni jankunne ne idan anyimaki daya saikiyi hankali Amman ayimaki harbiyu sai ancike sannan kidora hannu aka🙆🏿 kice nabani Na lalace Shin mezaisa kafin hakan tafaru kiyiwa kanki karatun tanatsu??? Ni mata kunabani mamaki dayawa sunsanifà Amman basa aiki dasanin saisuyi aiki dazuciya kusani duk wacce take aikida zuciya lallai zatakaita gahalaka imma mata imma mazà domin zuciya abokiyar shaidance bayada wajen zama facekusa da itah domin abukadan zairayamata yikaxa yikaxa Kuma kunsan shaidan baya sanyawa ayi alkhairi saidai akasin hakan idankuwà haryasakà kayi toyanada manufaryin hakan zai darsamaka abun azuciyarka dukdanfa kakauce hanya Ya Allah kakaremu damuda zuriarmu dagafadawa tarkon shaidàn kahana kunnuwanmu jinsautin kidansa Allah kakaremanà zukatanmu da imaniñmu Ameen Aisha✍🏼 ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠ Chapter 45 By Gentle Lady💃🏽 Mikewa tayi tahausaman tana kallonta ganin tahaye tamaza tawarware wani Dan kulli na magani tazuba daidai inda lubabatu tatashi tamiyarda kullin saitin zanenta takulle Tagyara zamanta tacigaba da shan ice cream dinta"" lubabatu tasauko tareda ice cream ahannunta taxauna tamika mata sanan tasamu guri tazauna suka cigaba da labari Ba ajima sosaiba lubcy tace barci takeji zataje takwanta" tayimata saida safe tahaura sama takwanta abunta Ita ma kaitsaye bangarenta tanufa tasake sheka wanka tadauko ragowar maganinda aka karbomata wajen boka tashaa babu jimawa dashansha taji kaman cikinta yasoma mirdawa Tadan dafe cikin zuwa cen saitaji tusa tadan karkace kafarta tusar tafito suutttt suuttt tasa hannu tana kore warin tusarr Ba afimintuna gomaba tasake dage kafaa tusar tafito buuuut buttt tayanzu tadara ta dazu wari sau hamsin Wanna karon saida ta Dade hancintaa"" motar Usman taji tashigo gidan dasauri tatashi tadage labule tareda fesa turaren daki Aranta tace danasani banci waken nan yaudayawaba gashi duk yabatamun ciki"" sannu sannu warin yafita koda usman yashigo kaitsaye bangarenshi yanufa Saida yayi wanka yashirya yayi bangaren lubcy yasamu tayi barcii saiyawuce bangaren samrat Yana saka kafarsa bangaren yaji wani bakon al amari wani shegen doyi kamar Yakoma saikuma yayi tamaza yashiga dakin tareda sallama Tanasaman gado tanata mutsuiniya domin wata tusar takeji Saman gadon yazauna yace nashigo yau bansameku a faloba" Tace ah wlh cewa tayi barciii takejii nikuma nagaji dazama nidaya shiyasa nadawo daki""" tamike dasauriii yace inazaki kuma??? Hartakai bakin kofa tace inazuwa Dan Allah harda dangudunta tasauko kasa tasaki tusarta tanata matsar ciki wai idan daragowar tusar tafito 😂nikuwa nace tusa bakashi bace samrat Tadanjima wajen sannan takoma dakin tareda ragowar warin"" bayan tazauna yasoma jinwani chanjii yadan bata fuska yace samrat wannan kuma warin menene??? Tunsanda nashigo nakejinsaa sama sama Tace eyem umm umm inajin berane yamutu adakin nan nima inajin warin sa sosai"" shiyasa naketa fesa turare tayi maganar tareda daukar tirare tasoma fesawa Yayimata kallon rashin yarda yace berah kuma samrat agidan nan ??? Tunda nake gidan nan bantaba ganin berah yashigoba Tayi saurin gwatseshi tace aishine dalilin dayashigo yasaka yamutu wlh berane maganarta tayi daidai dasurbuno wata tusar wacce batasan dazuwantaba Babu shiri Usman yadade hancinsa Yana kallonta yanda itama tarufe hancin yace umm lallai dole kirufe hanciii wannan shine beran dayamutu???? Tsuru tamasa da ido uwar kunya takamata"! Yace mekika cihaka samrat yabatamaki ciki??? Cikin jin nauyi tace wlh rabon ayi nadafa wake jiya nacikuma nasan bayashafamun lafiya batamun ciki yakeyi Yanisa tareda cire hannunsa daga kan hancinsa yace Amman dakin kirani kinfadamun aisai insiyomaki magan" kafin yakarasa furta magani tasake sakin wata Aibaisan sanda yazama natsayeba saigashi bakin kofa yacemata night baiko juyoba yawuce"" tayi tsuru yau Wake yatonamun asiri ina zaman zamana"" Turare tadauko takwanta dazaran barcii yasoma figartaa tasaki tusa tsabar warin tusar saiya farkarda itah Usman kuwa yanafita dasauri saida yakai bangarensa yasaki hannunsa dagakan hancinsa yaja iskaa yasaukarda ajiyar zuciya aransa yace wai ashedai tusar mata doyine da itah wannan abun aisaiya kashe mutum""" Yasake nisawa nikam bazankomaba dannima idan nayi wasa cikina zai lalacene gabanza"" dawan nan tunanin yakwanta yaukotakan abinci baibiba danyasan kodayacishi saiya amayardashi Bangaren samrat Kuwa tarasa dalilin bacin cikinta duk datasan wake taci amman warin tusar yayi yawa ahakan taketa fesa turere duk sa inda tayi tusar Kafin safe tiraren sanyaya dakin yakusan karewa""" washe gari tamakara koda tafarka takoma qalau fita tayi tayi break dantasan Usman yajima dafita Duk lokacinda yatunkari kofar dakinta warin tusar yakemasa maraba hakan yasaka yamadaina shiga tsayin kwana hudu batasakashi a idontaba Zaune take cikin falo damuwar rashin ganinsa tayimata yawa tana tunanin anya aikin boka yayi kuwa Kofar dakinta akaturo Usman ne cikin shigar kananun kaya sunyi masifar karbarsa"" yayikyau kuruciyarsa tadada fitowa Fuskarsa tana kumshe dawani sihirtaccen murmushi tsaye yayi bakin kofa yarungume hannuwansa yajingina dakofar yana jefanta dawani salon kallo nasoyayya maimatukar kashe jikin Wanda akayiwa Itakanta tayi mamakin ganinsa alokacin""" cikin sanyin murya tacemasa sannu dazuwa"" yace yauwa sammmratt yanda yaja sunanta harkarkashin zuciyarta tajiii talumshe idonta tabude tace ka karaso mana""" Kafada yamake yace bayan kinki kitaso kiyimun welcome bayankuma kinsan wajenki nazo"" tadan zaro ido tace nikuma??? Kaiyagyada ahankali yace sosaima inawajen aiki gabadaya narasa natsuwata jinake kamar zanhaukace idan bansakaki a idonaba Saiyanzu danaganki nasamu natsuwaa "" aranta tace wow maganina yafara aikii tayi Farida ido tace kaidai kodai wajen Antyna kazo Tsakiii yaja yace nibata gabana wlh nitunfarko danasan akwai irinki mezaikaini aurenta atsarina nibanason mace maikiba sannan banason macenda tafaye fari sosai nafison Dan daidai kamardai ke Yakai karshen maganar yanajifanta dawani kallo maisaukarda kasalaa"" itakuwa dadi duk yakumeta ganin tayi shiruuu yasaka yatako zuwa inda take yazauna juyoda itah yayi tana fuskarntarsa yace Yanaga kinyi shiru Tarausayarda kai bakomai yace so bawan nanba yanzu mekikeso ayi"" cikin shagwaba tace yawotakeso akaita yace bakida matsala tashimuje damakuwa ashirye take mayafinta kawai tadauka sukafito Falon kasa sukasamu lubcy tanaganinshi tace anzo gurin """ juyawa yayi kamar baigantaba saida samrat tace bakaga antyba??? Yace idanma nagantà mezanyi mata nibata gabana muje please" cikin murmushi tace Anty zamudanje yawo"" itama murmushin tamiyar mata tace tosaikundawo azomun dayan tsaraba Usman yaja dogon tsakii yawuce fuuuu samrat tawuce kandai kandaii ita aladole gamai miji saimundawo antyy Tace to adawo lafiyaa sunafita lubabatu tatintsire da dariya hartana tafa hannuwa saida tasoma hawaye Sunafita yan aiki sukafara kallonta da mamaki dama sunga lokacinda yashigo kuma yacemasu wajenta yazo Amman sundauka yayantane saigashi sungansu cikin yanayinda zainuna soyayya sukeyii Aisha✍🏼 ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠ Chapter 46 By Gentle Lady💃🏽 Hannunta tasagalo cikin nashi harsuka kai bakin motar""" yabude mata tashiga shima yazagaya yashiga sannan yatada motar" yayi hon maikulada get din yabude masu yafitaa""" Suna hawan titi tasukarda nannauyar ajiyar zuciya "" yakalleta yace yadai?? Talumshe ido tace wlh wani farinciki nakeji danasameka Yanakallon titi yace dagaske???? Tace sosaima kuwa"kaifa???? yacenima fiye dahaka wani dadine yakara kumeta Yace ina kikeso mufara zuwa???? Tace zoo yace angama""" gidan zoo sukafara zuwa ko ina tana makale dashii sunhadu damutane da dama harwadanda tasani tana gabatardashi amatsayin masoyinta abun alfaharinta Kamar suce to mijinkifa??? Saikuma sukyale yinin ranar sunyi yawo harsun gaji saigoshin magrib yadawo da irah gida yana saukarda itah yace zaije sallah nansuka rabu tayi cikin gida cikin yanga shikuma yakoma motarsa Yaja yafita yanahawan titi yabace batt dashi da motar"" dayake ranar baranar gurkinta bane wasa wasa kullum aljani usman saiyaxo suntafi yawon gari Tuni samrat takara kyau tayi haske abunta" abudaya yake damunta duk yanda tamatsu dason Usman yakusanceta yakii abun yasoma damunta Yaukam takuduri aniyar duk yazo sukafita saitasan yanda zatayi yabiyamata bukatar ta dawannan tunanin tawuni Yanazuwa kuwa tace yajirata tayi wanka tafito daga ita sai dangalallen towel saiwani kwarkwasa takeyi agabansa"" ido yakura mata shikansa tadimautar dashi Amman bazai safa alqawarinda yadaukarwa sugabansaba koda zaiyi hakan sai mijinta yagansu tare Duk yanda taso tadauki hankalinsa Sam baidamuba hartagama yau shigar kana nan kaya tayi sun bala in matseta komai najikinta anagani tadauko wani fitsitsin gyale tayafa tafesa turare wasu takalma masu matsakaicin tsayi tasaka"tajuyo takalleshi shimadin ita yake kallo tayi fardayan idanuwanta tace yakaganni???? Wow So beautiful"" kinganki kuwa tamkar wata tauraruwa gaskiya nayi dace dasamunkiii" tasake sakin murmushi tace tomuje sukafito tana makale da kafadarsa yanzu ko lubcy bataiwa magana suketafiya Bangaren Usman kuwa yauyakasa zaman office wata matsananciyar sha awa take damunsa saboda yakwana biyu baijegun samrat ba saboda doyinda yakeji Itakuma lubcy duk dayagano kalau take yashareta danyakudira aransa inhar ba itah tanuna tana ra ayiba bazaisake nemantaba abunda baisaniba lubcy ko ajikinta bataki suyita zama ahakanba Yaso daurewa Amman yaji ina Dan maararsa tamatsamasa key din motarsa yadauko tarreda turare domin yakare kansa da warin yasanarda ma aikatan wajen zaije yadawo Kaitsaye gida yanufa yayi hon maigadi yaduba yaga kowaye gabansa yafadi ganin Usman sannan yadawo dakallonsa ciki wajen samrat dataketa zubawa wani shagwaba Muryar Usman yaji yanacewa sani waime kakejirah??? Kabarni anan?? Cikin rudewa yabude masa kofar yanatunanin mekuma zaifaru yau Yanakunna hancin motarsa yagansu ido yazaro waje"" yanakallonsu da mamaki"" ahasale yataka burkii yafito kamar walkiya daidai zaibude mata mota sushiga Usman yadafe murfin motar yace malam wayekai??? Kuma mekakeyi anan ??? Mutumen yajuya wajen samrat yace wannan kuma waye??? Inakika kwasoshi??? Tashagwabe murya tace haba sweetyna ni inazansanshi yanda kaganshii nima hakan naganshi wlh bansanshiba Usman yayi kururuwa yachakumo wuyanta"" yashakee yace nikikecewa baki saniba to wlh yaukoni koke saina kasheshi mutumen yaturreshi dakarfii yace matar tawa zaka kashe??? Wlh dakuwa ka aikata babban kuskure barganin nakyaleka da itah tsawon lokacii inason matata"" Usman baki bude yake kallonsa yajuya wajen samrat wacce tamakale jikinsa yace kifadamun samira waye wannan??? Cikin daga murya tace mijina nemana maisona kuma maison farincikina"" saunawa zanfadamaka banasonka natsanekaa waimenene yakawoka gidan nan yanzu????/ Tsaki taja takalli mutumen tace mujeko sweety nagayana nema yabata mana lokacii wai ma inazamuje yau""" kaitsaye yacemata hotel tayi ihun murna yauwaa masoyina takaimasà sumbata akumatu sannan taballawa Usman harara shikuma yabudemata kofa tashiga yazagaya mazauninsa sai murmushi yakeyi yauyagama aikinsa yatada motar ganin basu bude get ba yasoma hon kafin yayunkura hartafito tace kai sani Dan iskanci baxaka budemana kofaba tsofaffun munafukai saura kukara gaba kuce kunga wani yazo gurinà tajatsaki takoma cikin motar sani jikinarawa yabudemasu yaharba motar kantiti tundaga Usman masu aiki dakuma lubabatu wacce hayaniyarsu tafito da itah tareda kawarta sajidaa tsaye suke kowa yana al ajabin wannan abun Usman kasa magana yayi raibace yawuce cikin gidan ko sannu dazuwan da lubcy takemasa bai tsaya amsawaba Shikam yaga jarabta duk macenda zai aurah saiyasamu sabani da itah haryau baiyi daceba Bangaren samrat kuwa sunafita Usman dinta yace wai waye wannan mutumen??? Baki tatabe tace barshi wani tsohon saurayinane wlh bansanma waye yanuna masa gidanaba murmushin gefen bakii yayi Kaitsaye wani babban hotel suka zarce Yakama masu dakii tundasuka shiga tamakalemasa damashi irin wannan ranar yakejirah yamorewa jikinta kafin yashanyemata jini Kaitsaye yasoma sunbatarta harsukakai kangado wani yanayi tasamu kanta acikinsa Wanda batasan konameyeba dagahaka batasake sanin komaiba Hayyanul zairi yakoma ainahin suffarsa ta jinnu sannan yakusanceta samrat batasan mekefaruwaba saida yagama abunda zaiyi sannan yadafata suduka sukabace Samrat sanyitaji yana ratsata ahankali tabude idonta cikin wani dajii tagansuu ga bokan akusa da itah zabura tayi tanajada baya tace kaiwaye??? Ina mijina??? Kodai Usman Dan yankan Kaine???? Bokan yakalleta ahasale yace wazai amsamaki wadan nan tambayoyin naki??? Kuka tafashe dashii tace Dan Allah karka cutardani banmaka komaiba kamiyardani inda kadaukoni Dariya yafashe da itah maitsoratàrwà dagabisani kuma saiyafasheda kuka maitsuma zuciyaa samrat abun yatsoratata tuntana jadabawa hartadake tamatso kusa dashii tace kaiwaye???mekakeyi anan Kuma meye dalilin kukanka da dariya alokaci daya??? Bokan baicemata komaiba saidayayi kukan mai isarsa sannan yadago yakalleta yace yake wannan yarinyar kisani bansan inane nanba dangane dani kowaye sanin hakan bazai amfaneki dakomaiba dalilin dariyata shine kekanki nalurah bakisan halinda kike cikiba dalilin kukana kuwa inatsoron namutu bansan mezan tarar acikin kabarinaba Tayi saurin tarar numfashinsa tace mezaisa bazaka sanardani kaiwayeba??? Yace saboda bazaki fita ananba kingakuwa babu amfanin kisanii Zaburah tayi tace mezakamun??? Kasheni zakayi??? Menaimaka tana maganar tana kuka kaiyagirgizà mata yace nikaina mutuwar zanyi mezan kàrudashi idan nakasheki???? Aisha✍🏼 ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠ Chapter 47 By Gentle Lady💃🏽 Tatsagaita kukanta tace wayene zaikasheka??? Batareda fargabar komaiba yace Wanda zaikasheki"" idanuwa tazaro waje tace laifin me kaimasu???? Yadanyi jim sannan yace sunana uwaisu nakasance nidayane awajen iyayena suna matukar sona sundauki son duniya sundora akaina bakamar mahaifiyata batason tagakomai yatabani Mahaifina baida hali sosai saidai yanada danrufin asirinsa kwatsam sai Allah yayiwa mahaifiyata rasuwa mahaifina ya auro wata azzalumar mace batada imani kokadan bata tausayina nikuma gani sangartacce bansan komaiba na ilimin boko ko arabiya Matar babana duk abunda takemun sainarama domin ni mugune Na iyah mugunta bana yarda kowa yacutardani dataga takasa komai dani harbokanta baiyi nasara akainaba saitasa mahaifina yaturani almajiranci Muna zaune asokoto sai akadaukeni akaturani Maiduguri nikuma tunda aka kaini sainafara biyar yara munazuwa yawo nasake hinjirewa inasake yinwayo mukaballe dawani yaro jabir zuwa tarabà Dagacen mukawuce jos yawomukaitayi harmuka samu wani boka yasoma koyamana bokanci"" abokina Wanda muke tare mundade muna harkar bokanci harmuka kware sosai saimukadawo zariya dazama Acikin wani jeji kusan duk dare mukan hadu muyi tadi dani dashi kusan abunda yarabani dagida nafada bokanci matar ubace shima haka Munakan haka saiyayiwa wata mata aiki itakuma kafin tayi aikin sai mijinta yakamata shine yatutseta saita sanardashi Wanda yayimata shine takaishi wajen abokina Dayaje yayimasa wa azi sai abokina yadaina wannan harkar kuma yasameni akogon danakeda zama yayimun nasiha dayake shiyafini ilimin addini danshi yanada sani sosai Nikuwa sainace nikam bazandaina harkar bokanciba saboda anan abincina yake sainayi amfani da maganar mutane dasuke cewa duk sana arda kasamu kanka acikinta to itah Allah yazaba maka Babuyanda abokina baiyiba domin ganardani harkarnan batada amfani kuma tanada hadari Amman nayi burus nasa auduga natoshe kunnuwana Daya nace yana fadamun Allah yace kaza yace kaza natashi afusace na soma tsibbona domin in halakashi saiyafara wadansu Abu yana daga hannuwa sama Sambansan meyake fadaba saidai nagane addua yakeyi domin natabajin malamin da aka kaimu makarantarsa yanayi take sainaga wata guguwa maikarfii tataso tarufemun ido Dani dakayan tsibbona aka watsamu gefe anan nasuma saidai nafarfado naganni yashe agefen kukar banga abokina jabirr ba"" yanisa daganan natattara nakoma ilori saboda nasamu labarin wani boka acen Acen nasake shahara da aikin bokancii lokacin natura aljani yadaukomun matar babana nadaureta akogon kuka nayita amfani da itah hartamutu nayihakanne domin narama cin mutuncinda tayimun Nadade INA aiki dabokan saiyazo yamutu dalilin mutuwarsa kuwa yajadawani bokane Wanda ake kirah *hatsabibin boka* shine yakasheshi yakwashe komai na sihirinsa nikaina nasamu labarin hakanne awajen wani aljanina kabusaa Daga lokacin saina tattara nadawo kaduna inamai bakinciki kuma naraya araina sainaga bayan wanann *hatsabibin bokan* nayiduk bincikenda zanyi domin nagane ainahin inama yakeda zama Amman nakaa duk bokancina bantaba ganin wani hatsabibi irinshiba yabatarda komai na sirrinsa babuwanda yasan takamaiman indayake saifa masuyimasa hidima cikin rawar murya tace tonikuma menaimashi???😨 Yace kishiyarki lubabatu itatace akasheki kirjinta tabuga tace matar Usman???? 😳Yace kwaraikuwa yacigaba Kwatsam watarana saiga mahaifiyarki tazonamaki aiki"" yanisa bansan kishiyarki tana daidagacikiñ masuzuwa wajen *hatsabibin boka*ba naimata aikii nafarko tabaki kekuma dake dakawarki kukaje wajen wani bokan Bayan bikinki dashi *hatsabibin boka* yaturo asanardani karnasake nasakeyimaki aiki kuma nawarware Wanda nayi danagane shine yakashemuñ ubangidana sainace aje afadamàsa bai isaba bazan bariba shikuma dayan bokan kawarkii yace yadainà yimàki aiki Nikuma danaso jayayya dashii aka daukeni zuwa kurkukunsa"" anata ganamun azaba damayausuke jirah suhadamu sukashee dani dake Yakai karshen maganar yana kallontà hannutadora akaitace nashiga uku lubabatu yazakimun haka"""🙆🏿 uwaisu yace kidaina kiran sunanta domin bazai amfaneki dakomaiba sai bakinciki"" Cikin kukatace kakirah aljanunka sufitardamu mana"" murmushin yake yayi yace dazan iyayin hakan danayi tun lokacindà nake kurkukunsa amman kisàni tunranarda abunyàfaru dukà aljanuna suka tsere yanzun haka sunkoma karkashiñsa Abokina jabirr yayi aure ya hayayyafa hayayyafa Yakoma wajen iyayensa yanzun nasan yama mantadani tundani nabijirewa umurnin ubangijina aidole inga badaidaiba😞 Samrat tace waikana nufin zaunawa zàkayi sukasheka??? Bayankuma munadà damar guduwa?? Kaga katashi mugudu danñibazan zauna akasheni abanzaba Yace karki wahaldà kanki wajen gudu danbazaki tsiraba abunda yafikawai muzauna mujirah mutuwarmu muguwar hààrara tasakar masaa tace ammankai bàhone wayafadamaka zañmutu ayanzu idanzakàje kataso Yace ah ah jeki abunkii ammankisani zakidawo"" tace saidaiwatà banibaa dama wandone ajikintà tatankwasheshi tàyañkii saitinda takejiyo wilgin motocii Aisha✍🏼 ☠ *HATSABIBIN BOKA!!!*☠ Chapter 48 By Gentle Lady💃🏽 Gudu takeyi kamar ranta zaifita Amman kokadan bataga alamun takusa kaiga titinba""" takara kadan kenan tacikaro dawadansu manyan namun jeji masu matukar girma dakuma tsoratarwa tunda take ko atarihi bata tabajin wadanda sukace sunga wannan namun jejinba Manyane tamkar giwa Amman kuma bagiwa bace sunada hakorah zagan zagan tamkar hakoran Damisaa harsundara nata dagirma dan tsayinsu zaiyi kamu hudu yawansu akalla sunkai su hamsin naman mutane suketa yagalgala kowa yanajan rabonsa sunayin arba da itah sukayo wajentaa Wani wawan burkii taci tajuya dagudu maimakon takoma inda tafito saitayanki gefen hagu da dajin tanagudu tana waige ganitake kamar baifi taku uku sukamotaba Gudu take tanakuka kamar ranta zaifitaa saikuma taji wata mahaukaciyar dariya gabadaya ta karade ilahirin dajin samrat bata daina guduba takusan shafe sa a daya tanagudu sannan tacikaro dawadansu manyan kunamai bakake kirin sukuwa wadan nan kunamai sunada wadansu faratai manya manya kamar fartanya "" da yatsunsu suke yagalgala naman mutum bawai dansuciba ga gawarwakin mutane nan bila adadin Tunkafin samrat takai gurin tajuyo dagudu tana mai danasanin barowarta wajen uwaisu gashi tawahala gabadaya Kuma hanya tabacemata tayama zatamaida kanta gunda yake Tanagudu tana kuka kamar ranta zaifitaa chak tatsaya sakamakon abunda tagani agabanta Wanda yafi dagamata hankali daduk abunda tagani abaya.. Wadansu manyan dodanni tagani masu matukar munin gaske kowanne daya girmansa yakai girman karamin daki dazaibude bakinsa bashakka mota zatasamu titi maikyau awajen "" . Idanuwansu manya manya kamar kwan fitila jajir dasu sunada farata irinna damisaa saitin bakinsu akwai wani tsinke mai matukar tsini Shisuke chakawa daidai saitin kwanyar mutum suzuke kwanyar kansaa saikaga yafadii ragab Daga gefensu akwai wasu tarin dodannin basukai wadancen girmaba dazaran wadan nan sunshanye kwanya sukuma zasu tsotse jinin jikinka daganan sujefawa wadansu dasuke bayansu gangar jiki Sukuma dasun jefomasu zasufara wawason naman jikinka wadansu sucire Kafa wadansu hannuwa wadansu kai kafin kafarga anyi gunsuwa gunduwa dakai tamkar sauroo wadan nan halittun sunada matukar munin gaske Dankuwa ganinsu kawai zai iyah haifarmaka da hawanjini sunayin arba da samrat sukayo cikinta dasaurii tajuya inda tafito tafi gwammacewa kunamu sukasheta da wadan nan dodannin sukamata Gudu taketayi tanahaki kwatsam saitaganta tadawo inda uwaisu yake yana zaune yanda tabarshii kusa dashi tafada tanahaki kamar wacce aka jefo Kuka tafashe dashi maiban tausayi"" uwaisu mezaiyi inba dariyaba yayi ta kyakyata dariya haryana hawaye yana buga hannu akasa tasharbe majina tana kallonsa Tace Yanzu uwaisu kana cikin wannan halin harkasamu damar yin dariya??? Hannuwa yayarbar yana kallonta yace to samrat mezanyi??? Konayi dariya konayi kuka nasandai sai ankasheni Tobagwanda indaraba inmore kafin namutu"" yanunata dayatsa yanacigaba da dariyarsa yace Amman meyadawo dake bayankuma kince bazaki dawoba?? Hawaye tashare tace wani bala in aiyadara wani nagwammace namutu anan din dakalar mutuwarda nagano acen kasan duk abunda kaga yakoro bera yafada wuta katabbar yafi wutar zafi Yatsagaita da dariyar sa yace kingano abundayafi nandin tashin hankaline?? Tace sosaima kuwa anan tasanardashi abunda tagano takarasa dacewa dan Allah kasamo mana Mafita mana domin mukubuta daga wajen nan Wlh koda banganiba nasan batasauki zasu kashemuba danbasuda imani tasake fashewa dakuka Uwaisu yace hanya dayace zata fitardamu idanhar mun iyah abunda malaman makarantar allo sukeyi addua kenan Tonikuma wlh ko alif bansaniba acikin adduar Amman tayiyu ke kin iyah maizaihana kiyimana kozamu tsira daga hannun wadan nan azzaluman Ido tazaro tana muzurai yace yadai samrat?? Tahadiye wadansu yawu masu daci tace wlh kilanta kwara kai kataba zuwa islamiyya nikam danake yargata agidan mu Iyayena masu kudine sosai danhaka basu damu dazuwana islamiyyaba saidai babana yadauko mana wani malami yana koyamana agida Dana kwatanci malamin zaizo sainashige bandaki bazansake fitowaba saina kwatanci yatafi babana baisan hakanba Mahaifiyata kuma babu ruwanta saboda itakanta batasan komaiba waccema takezuwa wajen boka atsammaninka tasan addini??? Saidai Duk abunda yashigemata duhu taje wajen boka tasanar dashi idan narantsemaka banyi karyaba ko alwala ban iyaba inadai wankawa inda naga mutane sunayi idankuma zanyi sallah bana karanta komai Saidai nakama dungura goshina sallar ma taganin damace danbanayi sai idan inaganin mutane kowajen buki dankar ace banasallah Amman yanzu rabona dasallah tunda nayi aure gashi lubabatu batayi itama dako awajenta zan iyah koya "" takai karshen maganar tana kallonsa Yace tokawai kigyara zaman jiran mutuwarki domin kuwa hanya dayace zata fitardamu yaukinga ranar zuwa islamiyya .. Yaune karatun islamiyya zaiyimana rana sanin dokokin ubangijinmu shine zai taimakemu adduar Neman tsari daga azzalumai bamu iyah komaiba Hakika mutuwace tadace damu domin kuwa rayuwarmu batada wani amfani nayi danasanin barowata makarantar allo a yau Samrat tace kadaina cewa mutuwarmu tafi amfani idan mukakoma gida aisaimushiga islamiyya Yayi murmushin yake dagabaya kenan aibakida wata dama niyanzu kallon gawarwaki nakemana kisani Allah yabamu damarda zamuyi aiki da itah domin neman ilimi Amman mukai watsi dawaccen damar Hausawa sunacewa idan kasamu rana tokashanya garinka niyanzu bansan iya adadin mutanenda Na haukatarba wadanda sukamutu tasanadina Bazan iyah kirgasuba"" nasan kema hakanne ta share hawaye yanzu kenan mutuwar zamuyii??? Yace bamakawa Kuwa"" tace yanxu lubabatuce tasakani cikin wannan halin laifin menaimata???wlh saina fadawa duniya abunda take aikatawa Uwaisu yatari numfashinta yace idan kinrayuko??? Karfa kimanta rayuwa guda dayace dazaran kinrasata shikenan duk Wanda yamutu bayadawowa Tasake fashewa dakuka tace idankuwa namutuuu anan wlh sainazama fatalwa nakasheta!!!! Aisha✍🏼 ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠ Chapter 49 By Gentle Lady💃🏽 Dariya yafashe da itah yace fatalwa ko?? Basai ruhin naki yatsira daga dukan da zakisha akabariba bari kiji kafin kedin kifadi hakan matar babana kafin tamutu saida tafurta hakan yafi sau ashirin Kisani wannan abunda yasamemu sakayyace tun aduniya munga sakamakon abunda muka dade muna aikatawa"" Wlh samrat alokacin bansan zanyi nadamaba bantaba kawo akwai wata rana dawani zaiganamun azaba makamanciyar wacce naganawa matar baba naba Arana daya nakan sadu da itah fiye dasau goma"" duk lokacinda naji bukata ta tasomun haka zanbiya bukata bayankuma nagama inyimata shegen duka Abinci kansa akasa nake ajiyemata saidai tarika cinta tanaci kamar dabba"" duk da itace silar lalacewata nasan nacutarda itah Saitayi kwana biyu banbata abinciba kuma baburuwana datana jini ahakan zanbiya bukatata da itah hartamutu nasa aljanu sukadauki gawarta suka kaiwa namun jeji Samrat tace Amman gaskiya kai bakada imani"" yakada kai yace bazan musamakiba dankuwa bansan ma menene imaniba"" dani dake aikuma duk daya tunda kema gashi son zuciya yakaiki ga halaka kema wayasan iya adadin wadanda kika kashe Shiru tayi tana kallonsa dankuwa maganarsa gaskiyace mijinda tafara aurah matansa biyu tazubawa guba sukaci suka mutu Tahaukatarda mata uku ciki harda Yar uwar mijinta dataga tasamata ido saigashi ya auro wacce tafita iyah hatsabibanci Itakuma duk datana magani kishinta yafiye yawa saigashi waccen tarinjayeta mijin yasaketa Allah mayasota bata kashetaba Tanisa hakane uwaisu nikaina nasan na aikata abubuwa Zaiyi magana tace mubar zancen hankalina bakwance yakeba inatunanin ta ina mutuwarmu zata riskemu agaskiya dazanfita anan akwai abubuwa dayawa dazanyiii Uwaisu yace duk cikin abunda zakiyi babu Na alkhairi "" takalleshi sabodame yasa kafadi hakan??? Yace saboda halin Dan Adam idan yashiga tashin hankali zaizubarda makamansa yayita Neman tsirah Amman dayatsira zakiga yawatsarda alkawullan dayadauka zaiyi Samrat batace komaiba"" shima uwaisu baisake maganaba duk abun nan dasuke aljani hayyanul zairi yanakusa dasu yanajinsu ammansu basa ganinsaa Wani kalloo yakebin samrat dashi yana lasar labba daganan yamike"" yatunkareta uwaisu kawai gani yayi samrat tafadii Tanata mutsuniya"" Gabansa yahau dukan uku uku dasaurii yamatsa bayaa"" tuntana motsi hartasuma"" take uwaisu yasaki fitsarii awando danyasan wajenshi zatazo yanzu"" Anyi akalla dakika hamsin dafaruwar hakan saiyaga tayi zumbur tamike tanaduban jikinta saikuma tafashe dakuka domin abunda taji kamar Wanda taji lokacinda Usman yake saduwa da itah a hotel Batagama tunaniba sukaji dariyaa takarade dajin takesuka hau waige waige"" dajin yasoma amsa kuwaa wata murya sukajii maikarfi dakuma kururuwa tasoma fadin "" kumore rayuwarku takwana uku kafin kumutu ayaudin nan nasokasheku. Kamar yanda shugabana ya umurceni amman ni imarda kejikinki wacce nadandana adaxu itace tahanani kasheku zanbarku zuwa kwana uku idan nagama morewa jikinki saina zukemaku jiniiii yasake haukacewa dawata dariyar Kuma zaku iyah gwada guduwa hanya abudeee take saidai kushirya ganin mugayen namun jejinda zakuhadu dasu karkuyi tsammanin zaku tsira danyanxu haka kuna karkashin wata duniyarne Yasake shekeewa da dariya saigawata iska maikarfin gaske tatashi tamamaye ilahirin dajinnn kukanta kawai zai iyah kurmantarda mutum Tsayin mintuna biyar guguwar talafa saigawani akushi shake da abinciii taredawani koko maidauke daruwaa yace ga abincinan idankuna bukata kokuciii kokuma kumutu dayunwaaa yanagama fadar hakan dajinnn yayi shiruuu Samrat taduke inda take tasoma darzar kuka itakam yanzu tagammace mutuwarta da rayuwarta Uwaisu ne yakaraso inda take yaduka yana kallonta yace dama kindaina bannar hawayenki dankuwa babu abunda kukanki zaijawo maki saiwani bakincikin Yajawo akushin gabansa yace kitaso muci abinciii idanuwanta tadago takalleshi tace abinci uwaisu??? Kaihar kasamu damar cinwani Abu??? Yaushe harzan iyah cinwani Abu"" uwaisu yakalleta da mamaki yace samrat kici kokarkici kasheki zaiyi kwarama kici kirage hasahi idankuma bazakiciba nizanci Dan bazanbari yunwa takasheniba Maganarsa tabawa samrat dariya tace karfa kamanta mutuwa zakayi ni danamutu hannun wannan marar"" imani wlh kara yunwa takasheniii Uwaisu shikam yasa abinci gabansa yaci mai isarsa"" ya turah sauran gefensa"" sannu kan hankali duhu yafarayi saihantar cikin samrat tasake duran ruwa tasan tabbas yau anan zatakwana"" Gefe daya tamakure gawani mugun sanyi gashi kayanta kananun kayane saiyanzu tayi takaici inama kayan kwarai tasaka sannu kanhankali akafara yayyafo masu kankara"" tuni hakoransu suka fara bugar najuna""" Usman tunsanda abun nan yafaru baisake lekowa wajeba"" dakinsa yashige kuma yarufe babu bugunda lubabatu batayiba danyabude Amman yayi banza da itah"" tagaji dankanta takyaleshi takoma wajen kawarta sukaciga ta maganarsu anan take sanarda itah ai aikin *hatsabibin boka* ne sajida tace haba dama naraya hakan araina sukataba sunamasu dariya Ranar Usman baiciko abinciba lubabatu dakinta takwana aranar"" washe gari takimtsa tajera abinci a dinner sannan tanufi dakin Usman""" Bangarensu samrat kuwa kwance nahangosu kamar gawarwaki saboda kankara tagama lullubesu""" ruwa aka kwaramasu masu zafiii wadanda sukai sanadin tashinsu gasanyi gazafiii Bayan kankarar tasauka dagajikinsu wannan karon ba samrat ba hatta uwaisu saida yafashe dakuka takekuma aljani hayyanul zairi yasoma bushewa da dariyar muguntaa Lubabatu tanashiga dakinsa tasameshi yagama shirinsa Amman yayi zaune yabuga tagumi shigowarta yasaka yadawo hayyacinsa Kusa dashi tazauna jiki asanyaye tagaidashi"" yasakar mata murmushi tareda amsa gaisuwarta"" yace kintashi lafiya tace qalau Sukai shiru sannan tace katashi ga abincinka yana jiranka"" danguntun tsaki yaja sannan yace wai zan iyah cin abinci wlh damuwa tayimun yawa Cikin alamar tausayawa tace kayi hakuri"" yanisa toyazanyi idan banyi hakurinba tunda banada naganin damuwata Rabona da farinciki tunsanda matata Dana aurah acikin mafarki tatafi tabarni wlh inajin kamar tatafi daruhina duk da mafarki ba gaskiya bane Amman nawa nakeganinsa kamar gaske inajikamar natabayin rayuwa da itah azahiri Haryanzu takanzomun amafarkina tanamun magana Amman dazaran nafarka zanmanta komai abudayane bana mantawa tanayawan cemun indage da addua rayuwata tanacikin hadari Ashe wannan abunne dazaisameni taketa nunamun"" lubcy wacce tasaki baki😮 cikin tsoro dafargaba aranta taçe kardai sotake tatonamun asiri!! Aisha✍🏼 ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠ chapter 50 By Gentle Lady💃🏽 Tsuru tayi tana saurarenshi ammanfa tashiga rudani dajin maganarsa dole tasanarda *hatsabibin boka* domin adakatarda itah Dan muddin tanazuwa masa watarana zata iyah fadamashi komai. Kuma duk ranarda hakan tafaru aikashina yabushe dannasan bazaikara zamadaniba"" Usman yace yadainaga kinshiga damuwa?? Tayi yake bakomai wlh damuwar kace tahaifarmun dahaka"" yasaki fara a yace gaskiya kinasona sosai tashi Muje indan tsakurah inwuce aiki yanajirana"" Tace to tareda mikewa sukajerah zuwa saman dinner din yadanci abincin balaifi, tarakashi yashiga mota saigakiran labila"" cikin fara a yadauka Yace yarleleta kina lafiya"" tace qalau dad ya kake tunjiya inata jiran naga kiranka Amman shiru banganiba harnakwanta""" Yadanyi shiru nadakiku uku tace yadai dad ko akwai wata matsalane??? Yace bakomai labila kidai tayani da addua inacikin damuwa wlh Shiru tayi aranta tace ga babbar damuwar nan ataredakai afilikuma tace dad kodai muzone??? Yalaso busassun labbansa yace ah ah dakinyi zamanki bafa wani abubane Tanisa shikenan dady"" hajiya suna gaisheka"" yace ina amsawa zankiraki anjima yanzun zantafi aikine inada meeting yau dakarfe shadaya Tace to Allah yabada sa a yace ameeen nagode tace love u dad"" yace mee2 takashe wayar tareda saukarda ajiyar zuciya Usman yabi wayarsa dakallo bayan yacirowayar daga kunnensa"" yamaida kallonsa wajen lubcy wacce take kallonsa yace natafi sainadawoko tace to adawo lafiya Tajuya cikin gida tana zancen zuci waiyanzu shikenan labila tayafeta tamkar ba itace tahaifetaba"" Yarinya saikace mai shafuwar aljanu hmm yanzu wamazaice nice mahaifiyarta""" tayi saman dakinta tanata surutu Bangaren su samrat kuwa tunlokacinda aka watsamasu ruwan zafi sukatashi idanuwa zuru zuru sai sukahau kallon kallo"" Take sukaji dariyar tacigaba da karade ilahirin dajin Uwaisu saiganin samrat yayi tafadi kamar jiya shidai jikinsa sairawa yakeyi gefe yakoma yanata makyarkyatar tsoro Saida yagama abunda zaiyi sannan tafarfado tanashan matukar wahala duk lokacinda yatara da itah saitagammace yamakasheta tahuta bayan ta farfadone yakawo masu abinci kamar jiya tace bazataciba uwaisu shikam yalakadi abunshi Zuwa rana dayasake Ku Santarta wannan karon kam dayakawo masu abinci saida taci danyunwarda taji saibayan tagama citadawo tanajin haushin kanta Dadare suna kwance akan gado lubabatu takalleshi tanasonyin magana tayi shiru yakurah dahakan yakalleta yace akwai maganane??? Tace ah yace tokifadamana inajinki"" tanisa dama zancemaka ne haryanzufa samira batadawo gidan nan ba"" Tagefen ido yakalleta sannan yatabe bakinsa yace to shine me??? Kokuma sokikeyi infita nemanta??? Danina aiketa?? Tace bahakan nake nufiba Amman ainaga matarkace tanada hakki akanka"" yasake mere baki yace aini tunjiya nagama da matsalarta takardar sakinta tana nan asaman gadonta dazaran tadawo zataganta"" Tanisa tanakallonsa tace nidai wlh inaji ajikina ba lafiyaba ina samirah zatashiga agarin nan kuma nakirah wayarta akashe take"" Guntun tsaki yaja yace aisaikiyi nidai karkidameni barci zanyi" idan abun yadameki saikitashi kije nemanta nidai kibarni inyi barci domin banida wata Alaka da itah"" Yanakai karshen maganar yajuya mata baya"" yaja mayafi yarufe jikinsa lubcy dariya tayi ahankali tayanda bazaijitaba sannan tajuya tayi barcinta Washe gari bayan yafita aiki "" saiga raliya tazo gidan saboda kwana biyu sunata Neman layin samrat basa samu"" tana shigowa suka gaisa da lubabatu tace tanaciki kuwa??? shiru tayi saida tasake tambaya sannan lubabatu tafada mata komai aikuwa tahau zage zage yanzu danrashin mutunci Kawata tabata agarin nan Amman kukasa zuwa cigiyarta??? Duk arzikin gidan nan saikacedai bamutum yabataba atunanina koda dabbace tabata aje nemanta ballantana mutum Lubabatu tace nikaina saida nayimasa magana tokinsan Abu bakaine kakeda ikon kankaba yace bazashiba ai itah bayarinya bace dazata bata Kuma bashine ya aiketaba"" raliya tarike kugu tace kicedai baida mutunci to wlh munfishi rashin mutunci kuma bari Kawata tadawo tadaina zama agidan sa dolene yabata takardarta kokuma hukuma tarabamu Lubabatu tace kwantarda hankalinki basaikunkai wajen hukumaba takardarta tana nan ya ajemata adakinta Bakisake raliya takalleta tace yasaketafa kikace??? Damuyake zancen tajuya fuuuu tafita tana sababi kaitsaye Dan adaidaita Tatara zuwa unguwarsu samrat Dama mamartane ta aikota tajiya maganar aikin yayikome dantun ranarda ta aikamata dashi tadainajin duriyarta Shine takirah raliya tadubomata itah saigashi tasamu wannan labarin gyalenta kawai tarida tadau jaka sukafita taja motarta zuwa dajinda boka uwaisu yake . Koda Suka karasa dajin saidai sukaganshi share babu ko alamar wani halitta yataba zama wajen sukayita tambaya a kauyukan dasuke makotaka da dajin Saidai akaimasu kwatancen wani bokan bayan sunfadamasa komai yayi yandubansa yace wannan aikin yanada hadari bazai iyaba"" dasuka matsa da magiya yace zaibada jininsu ga aljanu dole suka mike jiki bakwari wajen bokanda raliya tacezuwa wajensa sukaje shima yace wannan aikin yafi karfinsa"" sukaita yawo gidajen bokaye dayan bori karshe sukaje wajen wani boka nabakin rafiii bayan sunfadamasa bukatarsu yayimasu yandube dube yace tana raye Amman batacikin wannan duniyar"" hajiya tace kataimaka konawa kakeso zanbaka indai yata zatadawo"" yace karkidamu za ataimaka yasanarda itah turarenda zatakawo dakuma kaji dansai anyi yanka aikine mai wahalar gaske dakuma hadari tace Itah konawane zatakashe inhar yarta zatadawo yace takwantarda hankalinta takoma gida takwanta yarta' zatadawo hargida tace tozata bada kudin aikin saiyasaka asiyomasa komai yace badamuwa haka tazube masa bakin aljihunta sannan sukadawo gida hankalinta kwance Bayan kwana hudu dabatan su"" darana suna zaune duk sun rame sun lalace fargaba dakuma tashin hankali saboda tunranarda aka kaisu dajin kullum kafin safe kankara saita daskaresu saida safe atayardasu daruwan zafiii yaunekuma adadin kwanakinda yadibarmasu"" suncika"" saiyan dube dube suke suga ta inda mutuwar zatabullomasu wata iska sukaga tataso maikarfiii tayiiii samaa wani duhu ya mamaye ilahirin saman dajin take hadari yahadu yayi baki kirin anata tsawa mai firgitarwaa!!! Kuyi hakuri wlh bansamu damar yin typn dinba kuyi hakuri da wannan Aisha✍🏼 ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠ chapter 51 By Gentle Lady💃🏽 Tuni uwaisu yasoma sakin zawo" sabanin samrat datasoma kuka tanakiran wayyo yanzun mutuwa zanyi Sunacikin wannan yanayi akasoma huromasu iska tamkar ruwa tafashasshi suna suraci take. Fatar jikinsu tasoma dayewa dakanta"" Dasauri uwaisu yaruga domin yadimauce dayanayinda yakeji ajikinsa"" ganin hakan yasa samrat tabishi sukaita gudu Guguwarce tatari gabansu take tadauke uwaisu saigashi yana shillo acikin iska tamkar guguwa tadauko karmami"" samrat tasake kwalla karaaa Amman takasa guduwa uwaisu kam sai witsil witsil yakeyi da kafaa Zuwa mintuna biyar akasauko dashi yafadi ragajab babu rai ajikinsaa idanuwansa sun kakkafe harshensa yafito waje Wannan yanayin yasake firgita samrat dagudu tajuya tanamai kuka tanawaige waikar itama azo gurinta"" tayi gudu mai nisa daga inda gawar uwaisu take cikibis tayi da usman yashigo jejin Dasauri tayi wajensa tafada jikinsa tanakuka tace Usman kafitardamu wajen nan wlh mugayene kashemu zasuyi"" Hannunsa yasaka yasoma bubbuga bayanta ahankali cikin rarrashi"" tasake shigewa jikinsa tana saukarda ajiyar zuciyaa Hannuwansa dasuke cike da kumba "" yasoka mata tacikin bayanta take tagantsaraa idanuwanta suka ganomata usman bakinsa duk yabaci dajini Kafin tayi wani yunkurii yashanye jininta duka saidai kawai gawarta yayar yakoma guguwa zuwa inda ya aje gawar uwaisu yadaukota sannan yadawo yasauki dawar samrat yatashi sama yabace cikin gajimare Yau tsayin sati daya maman samrat hankalinta yaki kwanciya kullum takwanta barci saitayi mafarkin samrat tanakuka tanacewa mom yanzu harkinada lokacin kwanciya ??? Nikuma ganinan inashan azaba akan abunda Na aikata aduniya Duk abunda yafaru dani mom kece sila tunda kika kasa tarbiyartar dani akan addinin Allah ban iya sallah ba bansan yazan bautawa ubangijinaba Kisani duk bala inda zanshiga kema kinada linkin nakii yana nan yanajiranki"" hannunta tasaka tace mom shigo ciji zafinda nakeciki tayi maganar tanariko hannunta Aituni takwallah wata mahaukaciyar Kara tatashi firgigit tasoma bin hannunta da kallo Wanda yayi jajir saboda zafindake jikin samrat datarikata""" Sai zazzare ido takeyi kamar wacce tai karya jikinta yahaubari dasauri tasauko dagakan gadon tayi waje Falo takoma tazauna tanata fiffita jikinta wannan wace irin masiface kai anya mafarkin nan bagaske bane???? tarike baki komadai watace takeson korana gidan nan shine tabiyomun tahanyar yata dantaga bayana Kai aizama baiganniba tamike dasaurii takoma daki tawanko fuskarta tasake shiga tadauki kudi da key din motar ta tayi hanyar dajinda bokanda aka kaisu da itah da raliya Kodataje tasameshi yana ganawa dawata hajiyar bakin Yar bukkarsa tatsaya""dantasamu bukkar andan sakayata kuma taga mota bakin bukkar hakan yasa tatsaya domin tajirah Tayi tsayin awa uku awajen sannan taga anbude bukkar saiga matar tafito tana gyara daurin zanenta da mayafi tanacewa saiyaushe kuma boka??? Shikuwa yana lasar baki yace kidawo zuwa jibi yamaki ko??? Tace haba boka ai wlh koda kullum kace indawo indai hakan zaihana mijina kwasomun wannan tsinanniyar wlh zanyii Yawashe hakorah karkidamu hajiya aitunda akai wannan aikin mijinki bashi bakoma saduwa dakowace mace matukardai yakusanceki aduk lokacinda akaimaki wannan aikin Yanzu anyi sau uku sauran bakwai Dan aka idar aikin sau goma akeyinsa daga lokacin da aka kammala aikin shikenan kisamu waje kibarje guminki dankuwa babuke bakishiya saidai kiji sunanta awani gurin badai agidankiba!! Tawashe baki godiya nakeboka sainadawo jibin ta bude kyauren tafito sukaiwa juna kallon kallo da itah da maman samrat tawuce abunta itakuma tarakata da ido ganin babbar mace maijidakanta ta iyah kwanciya dawannan kazamin baki duk goro Wanda bayawanka bakinsa baitaba samun wankiba"" Matar babbar motarta tashiga tajata tawuce ko kallon indatake batayiba"" sai alokacin tasaukarda ajiyar zuciya taturah kyauren kofar tashiga Yanazaune yamike kafarsa saiyanxuma yake gyara daurin zariyarsa yana sharce zufa"" tayimasa gafaradai yace takaraso nesadashi tazauna danwani mugun kyankyaminsa takeji Yayi yanzane zanensa sannan yadago yacemata meke tafedake??? Cikin muryar damuwa tace akan maganar yata wlh nayi mummunan mafarki akanta yaudin nan"" tasanardashi mafarkinda tayi Tanagama fadamasa yasheke dawata irin dariya wacce tasaka hanjin cikinta murdawa"" saida yagama dariyarsa sannan yace bahakan mafarkinki yake nufiba kisani mijinki yanason karo aurene!! Gabanta yayanke yafadii Yacigaba yarki tana nan raye Amman tanacikin wani halii yauyau nakeson tura aljani yadaukota kudin aikinkine sukai kadan aidatuni tadawo Tace haba boka aiyakamata kafadamun konawane nizan iyah bayarwa "" tanisa toyamaganar kuma yarinyarda maigidana yake nema???? Yayi kaki yatofar yace tana nan amman kuma zamuyima tufkar hancii yanzu zakibada dubu Dari uku danaki danata saboda aikin akwai wuyaa Tayi shiru sannan tace to gaskiya dari biyune nazodasu saidai idan zakabini gobe gobe zankawomaka yace shikenan Amman kitabbatar kinkawo dankonairah idan babu aikin nan baxai yiyuba tace zankawosu gobe gobe Yace shikenan tazube kudin tatafi tazubeduka kudin Jakarta sannan tawuce zuwa gida tanaxancen zuci wato baban samrat aure zaikara Amman shine kullum yake lullubeta da dadin bakii humm hartakai gida tana tunanin"" Dadare dukkansu sunacikin falo suna sauraren tashar labarai"" tanagefe zaune danhaushin baban samrat takeji"" Salatinda taji yanayi yasaka itama takai dubanta akan TV gawarwakin wasune subiyu akan mota sunkunburah kuda saibiyarsu sukeyi Daidai akanuno fuskar samrat gabadayansu sukamike suna rabka salati banda mamanta datadorah hannu akatarabka ihu nashiga ukuna asheda gaskene kinmutu??? Baban samrat yabita dakallo cikin mamaki yajuya wajen yayunta yace sutashi yanzun suje asivitin Babu bata lokaci yaso sosai sufara biyawa tagidan Usman"" saiyayyunta sukace sufara daizuwa su tabbatar inhar itane Dasukaje kafinma abarsu suga gawarta saida suka wahala"" sungani kuma suntabbatar itace tomeya hadata dawannan mutumen gashikuma bamijinta bane??? Yayanta ayuba yace subari saigobe dankuwa baza abasu gawarba zuwagoben da sassafe suje gidan Usman din hakan akayi ammanfa Daren babuwanda yarumtsa musamman mamanta dataketa kuka Washe gari ayubanne yajegidan Usman maigadi yafadamasa ana masa sallama yayi mamaki wazaizo nemansa irin wannan lokacin tunda yatunkaro yagane kowaye saiyasha toka Yakaraso yabashi hannu suka gaisaa ayuba yace yagidan?? Usman yace lfy""" Ayuba yanisa yace dama nazone akan maganar Kanwata tunkafin yarufe baki Usman yace Toni inaruwaana duk abunda yasameta karku nemeni"" bakisake ayuba yakalleshi saida yakai karshe yanisa yace Amman Usman banji dadin abunda kafadabà yarinyar nan matarkacefa??? Yayi saurin tarar numfashiñsà yace adaba aini nadade dasakintaa yanzunhaka jiranake kawai tadawo wajen kwartancinta taxo takwashemun kaxaman kayanta daga gidana Ayuba yace kasaketafa kace??? Yace kwaraikuwa kumabata gidana danrabontà dagidannan sati daya hardakwàna biyu Ayuba yace ammandai kàibakàsan mutunciba Aisha✍🏼 ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠ Chapter 52 By Gentle Lady💃🏽 Yanzun ace samirah batagidan nan tsayin sati dakwana biyu Amman kakasa Neman mu kasanardamu... Wani mugun kallo yawatsa masa yace dayake Nina aiketa ko anfadamaka ni Dan aiken kune dazanje insanardaku inda take Duk gidan ubanda taje nibandamuba idan kunganta kufadamata tazo takwashemun kayanta daga gidana tunkafin nasaka yara suyimun waje dasu Maganar Usman tatunzura ayuba Duk dayana ganin Usman babban mutum ne baihanashi kaimasa dukaba saboda bacin rai Usman yayi saurin tare dukan"" dadaya hannunsa yarike hannun daya yawanka masa mari"" yace kaiharka isah kazo gidana kace zakadakeni?? Aikuwa fadane yakarke tsakaninsu sukasoma jefar juna damasifa kamar zasubuga maigadine da driver sukayo wajensu sunajaye ayuba Yatuge hannunsa daga rikonda yamasa yace badai nikamaraba wlh kabar takamar ganin kanada kudi sainadaureka komai dukiyarka bakin azzalumi Anaganinka da suffar babban mutum ashekai bakasan mutunciba"" Sunday yarikeshi yace karfa kaga lefin alhaji saboda balaifinsa bane agabanmu akai komai"" Usman yacewa Sunday kubarni dashi nizanyi maganinsa wlh bari nafito yayi cikin gida dasaurii Sunday yaja hannun ayuba yace kazo kafita tunda har kaga ran Alhaji yabaci komai zai iya yi Shikuma yace babu inda zaije saidai idan kasheshi zaiyi yakasheshi danshi baya tsoronsa Dakyar sunday da sauran ma aikatan gidan sukafita da ayuba lokacin Usman yafito da bindigarsa kamar wani mahaukacii Hayaniyar suce tafargarda lubabatu aitana jin masu aiki suna fadar bindiga dagudunta tahau saman tadauko kwalbar tasassautoda kullinda taimasaa Dasaurinsa yatunkari kofar fita ana rirrikeshi dankuwa jiyakeyi zuciyarsa tanata tafasa masu aikin suna rirrikeshi yana turesu"" Lubabatuce tafito dasauri tarike bindigar yajuyo afusace yakalleta cikin sanyin murya tace kayi hakuri Dan Allah alhajii Saiya sakarmata bindigar yajuya fuuuu cikin gida tajuya tabi bayanshi Sunday kuwa sunafita yasanarda ayuba duk abunda yafaru gabadaya jiyayi kunya tarufeshi Dangabadaya masu aikin kowayace hakan akayi harma sukafadi Wanda sukasani Wanda akai ba agaban Sunday ba"" sunday yace babban tashin hankalin yanzu ba asan inda takeba dantunda tabar gidan alhaji batadawoba"" jiki asanyaye yace aitarasu gabadaya sukace tamutu??? Yagyada kansa yanzun abunda yasaka nazoma sanardashi gawarta tana mutuware "" gabadaya sukai zugum yace damuna mamakin waye take taredashi Ashe dama samira tana Neman mazane da aurenta??? Yashare sirarun hawayenda suka saukomasa yabar kofar gidan zuwa asiviti""gabadaya sukabishi da kallon tausayawa suna jinjina Kansu Dayaje asivitin suka tambayeshi Usman yafadamasu komai kowannensu jikinsa yamutu saikusan azahar akabasu gawar bayan sunzube masu kudi dubu talatin Aranar akaimata sallah aka kaita makwancinta"" Usman Sam baiji labariba saida aka sake kwana biyu Sunday yake sanardashi Dayafadawa lubabatu tayita kuka hartabashi haushi"" saida taje tayimasu gaisuwa Amman Usman kinzuwa yayi"" saboda kunyar abunda yayiwa ayuba saida gabaya yajibai kyautaba Tundaga lokacin Mamar samrat takoma saliha kullum kasameta rike da charbii tasaka akanemo mata wani malami yana karantarda itah Su hajiya sunsamu labarin sukaimasa gaisuwa dakuma fatan Allah yabashiwata tagari labila kam wata tsanar mamanta tasakeji tundaga lokacin Usman yacire sha awar aure aransa saidai yaje asiviti yasiye magungunan da zaisha domin yarage yawan sha awa Idankuma tatasomasa saiyasha maganin "" tsayin shekara daya"" dafaruwar hakan watarana dayaziyarci family doctor dinsu akano akan ciwonda yake damunsa A mararsa yanzu takaima idan yasha maganin baya masa amfani"" saboda yanada tsananin bukata kuma lubabatu babu abunda yasauya awajenta domin sukan kwashe sati biyu bata yarda yakwanta da itah ba Kuma idan tace bataso dolensa yakyaleta"" suna office din doctor din bayan yagama yimasa bayanin komai yana kallonsa saida yakai karshe yanisa Yace wannan laifinkane alhaji batunyauba nake sanarda kai shan wannan maganin bazaiyiba kawai Kayi aure shine kawai Mafita Tunda kanada kudinka ballantana kace bakada kudin auren"" Usman yace doctor bakagane abunda nake guduba wlh niyanzu tsoron aurema nakeji saboda halin matan bawai banada kudin auren ba Alhamdulillah Amman matanne nayanzu kafin kasamu takwarai sai kahawala Doctor yayi murmushi yace hakane Amman kasan ba ataruwa azama daya dole akwai nakirki nidai shawararda zanbaka kagaggauta yin aure Dan maniyyi yatararmaka amara"" yanason fita kuma saika guji cinkayan dadi masu saka maniyyinka kara yawa"" idan bakai wasaba wannan abundakake dauka bawani abuba zaijawomaka kwanciya asiviti Usman yayi shiru nawadansu dakiku sannan yanisa yace shikenan zanyi inshaa Allah katayani da addua"" yace karkadamu sukai sallama yawuce gidan hajiya Labila Batasan dazuwan saba dantana gidan sahiba"" damadai bajimawa zaiyiba yabarwa hajiya sakonta yawuce Wannan shawarar Usman yayi aiki da itah Amman abun mamaki dazaran yasamu wacce yayaba da hankalinta sai magana ta kankama yarinya tace bataso tasamu wani said ayanemi yarinya hudu kowacce hakanne tahudu saima da akabiya sadaki tace bataso da iyayenta suka matsamata ganin alhajine maikudi ta nanewa wani talaka sanadin hakan yasaka tashiga duniya Su awajensu tabijirewa umurninsu basu saniba aljanine ake turomasu basune suke furta hakanba"" Usman kullum zakasameshi masallaçi gayawan azumie alokacinne Sunday ya musulunta""" sannu sanñu abunyasoma damun Usman saiya sanarda dahiru abokinsa"" Dahiru ne yahadashi da habiba"" wacce ya aurah daga karshe yargidan mutunci saigashi batadibo da yawaba tarigamu gidan gaskiyaa *CIGABAN LABARI* Lubabatu saman gadonta tahaye tadauko madubintaa tashafo tareda kiran sunan hatsabibin bokaa shafawarta keda wuyaa saigashi yabayyana kamar kullum Kirari tasomayimasa tanafasa masa kai yasaki wata shu umar dariya""" itakanta saida tatayashi tace boka aiki yayi kyau saidaikuma maganar yata labila take takenta yasoma isata nifa inagudun watarana tatonamun asiri yarinya kamardai banice nahaifotaba kodaya batabiyo halinaba *hatsabibin boka* yatsagaita da dariyarsa yace waimeyasa kike shakkune akan aikina" narantse dagirman tsafina babu wani mahakulinda zai iyah fallasa asirinki tundahar kikahada damu bakida sauran bakinciki yarki kuma kimanta da itah komai kikaga tanayi kisamata ido zata iyah fadamaki magana Amman bakinta bazaibata iyah furtawa waniba kodataso fadadin Tasaki murmushi godiya nake boka toyanzu mezanbayar amatsayin kyautar murna??? Yace abunda kikasaba bayarwa"" tace to gobe zakagansu takehasken yafito tajikin glass din boka yabace tamiyarda madubin cikin jindadi Aisha✍🏼 ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠ Chapter 52 By Gentle Lady💃🏽 Yanzun ace samirah batagidan nan tsayin sati dakwana biyu Amman kakasa Neman mu kasanardamu... Wani mugun kallo yawatsa masa yace dayake Nina aiketa ko anfadamaka ni Dan aiken kune dazanje insanardaku inda take Duk gidan ubanda taje nibandamuba idan kunganta kufadamata tazo takwashemun kayanta daga gidana tunkafin nasaka yara suyimun waje dasu Maganar Usman tatunzura ayuba Duk dayana ganin Usman babban mutum ne baihanashi kaimasa dukaba saboda bacin rai Usman yayi saurin tare dukan"" dadaya hannunsa yarike hannun daya yawanka masa mari"" yace kaiharka isah kazo gidana kace zakadakeni?? Aikuwa fadane yakarke tsakaninsu sukasoma jefar juna damasifa kamar zasubuga maigadine da driver sukayo wajensu sunajaye ayuba Yatuge hannunsa daga rikonda yamasa yace badai nikamaraba wlh kabar takamar ganin kanada kudi sainadaureka komai dukiyarka bakin azzalumi Anaganinka da suffar babban mutum ashekai bakasan mutunciba"" Sunday yarikeshi yace karfa kaga lefin alhaji saboda balaifinsa bane agabanmu akai komai"" Usman yacewa Sunday kubarni dashi nizanyi maganinsa wlh bari nafito yayi cikin gida dasaurii Sunday yaja hannun ayuba yace kazo kafita tunda har kaga ran Alhaji yabaci komai zai iya yi Shikuma yace babu inda zaije saidai idan kasheshi zaiyi yakasheshi danshi baya tsoronsa Dakyar sunday da sauran ma aikatan gidan sukafita da ayuba lokacin Usman yafito da bindigarsa kamar wani mahaukacii Hayaniyar suce tafargarda lubabatu aitana jin masu aiki suna fadar bindiga dagudunta tahau saman tadauko kwalbar tasassautoda kullinda taimasaa Dasaurinsa yatunkari kofar fita ana rirrikeshi dankuwa jiyakeyi zuciyarsa tanata tafasa masu aikin suna rirrikeshi yana turesu"" Lubabatuce tafito dasauri tarike bindigar yajuyo afusace yakalleta cikin sanyin murya tace kayi hakuri Dan Allah alhajii Saiya sakarmata bindigar yajuya fuuuu cikin gida tajuya tabi bayanshi Sunday kuwa sunafita yasanarda ayuba duk abunda yafaru gabadaya jiyayi kunya tarufeshi Dangabadaya masu aikin kowayace hakan akayi harma sukafadi Wanda sukasani Wanda akai ba agaban Sunday ba"" sunday yace babban tashin hankalin yanzu ba asan inda takeba dantunda tabar gidan alhaji batadawoba"" jiki asanyaye yace aitarasu gabadaya sukace tamutu??? Yagyada kansa yanzun abunda yasaka nazoma sanardashi gawarta tana mutuware "" gabadaya sukai zugum yace damuna mamakin waye take taredashi Ashe dama samira tana Neman mazane da aurenta??? Yashare sirarun hawayenda suka saukomasa yabar kofar gidan zuwa asiviti""gabadaya sukabishi da kallon tausayawa suna jinjina Kansu Dayaje asivitin suka tambayeshi Usman yafadamasu komai kowannensu jikinsa yamutu saikusan azahar akabasu gawar bayan sunzube masu kudi dubu talatin Aranar akaimata sallah aka kaita makwancinta"" Usman Sam baiji labariba saida aka sake kwana biyu Sunday yake sanardashi Dayafadawa lubabatu tayita kuka hartabashi haushi"" saida taje tayimasu gaisuwa Amman Usman kinzuwa yayi"" saboda kunyar abunda yayiwa ayuba saida gabaya yajibai kyautaba Tundaga lokacin Mamar samrat takoma saliha kullum kasameta rike da charbii tasaka akanemo mata wani malami yana karantarda itah Su hajiya sunsamu labarin sukaimasa gaisuwa dakuma fatan Allah yabashiwata tagari labila kam wata tsanar mamanta tasakeji tundaga lokacin Usman yacire sha awar aure aransa saidai yaje asiviti yasiye magungunan da zaisha domin yarage yawan sha awa Idankuma tatasomasa saiyasha maganin "" tsayin shekara daya"" dafaruwar hakan watarana dayaziyarci family doctor dinsu akano akan ciwonda yake damunsa A mararsa yanzu takaima idan yasha maganin baya masa amfani"" saboda yanada tsananin bukata kuma lubabatu babu abunda yasauya awajenta domin sukan kwashe sati biyu bata yarda yakwanta da itah ba Kuma idan tace bataso dolensa yakyaleta"" suna office din doctor din bayan yagama yimasa bayanin komai yana kallonsa saida yakai karshe yanisa Yace wannan laifinkane alhaji batunyauba nake sanarda kai shan wannan maganin bazaiyiba kawai Kayi aure shine kawai Mafita Tunda kanada kudinka ballantana kace bakada kudin auren"" Usman yace doctor bakagane abunda nake guduba wlh niyanzu tsoron aurema nakeji saboda halin matan bawai banada kudin auren ba Alhamdulillah Amman matanne nayanzu kafin kasamu takwarai sai kahawala Doctor yayi murmushi yace hakane Amman kasan ba ataruwa azama daya dole akwai nakirki nidai shawararda zanbaka kagaggauta yin aure Dan maniyyi yatararmaka amara"" yanason fita kuma saika guji cinkayan dadi masu saka maniyyinka kara yawa"" idan bakai wasaba wannan abundakake dauka bawani abuba zaijawomaka kwanciya asiviti Usman yayi shiru nawadansu dakiku sannan yanisa yace shikenan zanyi inshaa Allah katayani da addua"" yace karkadamu sukai sallama yawuce gidan hajiya Labila Batasan dazuwan saba dantana gidan sahiba"" damadai bajimawa zaiyiba yabarwa hajiya sakonta yawuce Wannan shawarar Usman yayi aiki da itah Amman abun mamaki dazaran yasamu wacce yayaba da hankalinta sai magana ta kankama yarinya tace bataso tasamu wani said ayanemi yarinya hudu kowacce hakanne tahudu saima da akabiya sadaki tace bataso da iyayenta suka matsamata ganin alhajine maikudi ta nanewa wani talaka sanadin hakan yasaka tashiga duniya Su awajensu tabijirewa umurninsu basu saniba aljanine ake turomasu basune suke furta hakanba"" Usman kullum zakasameshi masallaçi gayawan azumie alokacinne Sunday ya musulunta""" sannu sanñu abunyasoma damun Usman saiya sanarda dahiru abokinsa"" Dahiru ne yahadashi da habiba"" wacce ya aurah daga karshe yargidan mutunci saigashi batadibo da yawaba tarigamu gidan gaskiyaa *CIGABAN LABARI* Lubabatu saman gadonta tahaye tadauko madubintaa tashafo tareda kiran sunan hatsabibin bokaa shafawarta keda wuyaa saigashi yabayyana kamar kullum Kirari tasomayimasa tanafasa masa kai yasaki wata shu umar dariya""" itakanta saida tatayashi tace boka aiki yayi kyau saidaikuma maganar yata labila take takenta yasoma isata nifa inagudun watarana tatonamun asiri yarinya kamardai banice nahaifotaba kodaya batabiyo halinaba *hatsabibin boka* yatsagaita da dariyarsa yace waimeyasa kike shakkune akan aikina" narantse dagirman tsafina babu wani mahakulinda zai iyah fallasa asirinki tundahar kikahada damu bakida sauran bakinciki yarki kuma kimanta da itah komai kikaga tanayi kisamata ido zata iyah fadamaki magana Amman bakinta bazaibata iyah furtawa waniba kodataso fadadin Tasaki murmushi godiya nake boka toyanzu mezanbayar amatsayin kyautar murna??? Yace abunda kikasaba bayarwa"" tace to gobe zakagansu takehasken yafito tajikin glass din boka yabace tamiyarda madubin cikin jindadi Aisha✍🏼 ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠ Chapter 53 By Gentle Lady💃🏽 Yanzukam Usman yafitarda rayuwar kara aure yabarwa Allah zabinsa yasan wannan jarabtace Allah yabashi ikon cinye wannan jarabawar Zaicigaba da azumie yakumaci gaba dashan magani idankuma harciwon yacijikinsa inkwanansane yakare to Allah yajikansa Tuni yakauda kai gadukkan abunda yasan zaitadomasa da sha awarsa gabadaya company nsa yasallami ma aikatansa mata baibar kodayaba bayan yabasu makudan kudi yace sunemi wani aikin daban sosai sunji bakinciki dankuwa babu inda ake biyan su albashi mai gwabigwabi sama da wannan company sosai maishi yasan darajar aiki dakuma biyan ma aikata kudinsu akan kari kuma amutunce Baibar mace kodayaba yasaka duka maza"" duk satii saiyayi sadaka yana Neman Allah ya bashi lafiya" Yakuma yayemasa damuwàsa Zaune yake cikin falonsa sama lubabatu tana gefensa suna kallo wayarsace tahau ringing"" tana gefensa yanadubawa yaga labila cikin fara a yadauka Tareda sallama ta amsa adaya bangaren"" tace dad Barka dadare??? Yace yauwa kina lafiya?? Tace qalau nake dad fatan kaima hakan?? Yanisa insha Allah "" yakaratun??? Shekaranjiya ainakirah akacemun kina makaranta wajen harda" tace wlh kuwa dad abunda yasakama nakiraka kenan Yagyara zama wani abunne??? Tace ah maganar walimarda za ayi makarantarmu tawadanda suka hardace AlQur'ani dakuma wadanda suka sauke Hardar mataki matakine akwai masu hizifi sittin akwai arba in akwai talatin akwai masu a shirin goma dakuma biyar Daga kowanne aji ni inacikin masu arba in" yace masha Allah godiya tatabbata ga Allah madaukakin sarki Allah yataimaka tace Ameen"" wlh naji dadi sosai labila yaushene walimar??? Tace saurah satii uku Amman Dan Allah dad wannan karon kazo yace karkidamu zanzo "" tamarairaice fuska kamar zatayi kuka race sanda nasauka bakazoba ai"" Yace sha kuruminki wannan karon koda tafiya takamani zansoke tafiyar indai zuwan nawa zaisa amanta dawancen laifinda nayi Dariya tayi tace bakayi laifiba ai kawaidai naga kowacce mahaifinta yanazuwa mata"" yace aikema haka baga uncle Hafiz nanba Taturo baki nidai dad ah ah kainafison kazo inaso naganka"" yamurmusa tokarki damu zanzo dame dame kike bukata zan aikomaki dakudi saiki siya"" Tace la dad damakabari wlh uncle yasiyamun komai harnakai ankon wijin dinkii"" yace duk dahaka ni ai yakamata nabada tawa kyautar Tace hakane to dad kabani duk abunda Allah yahoremaka komenene zanji dadi"" yace dagaske??? Kaita gyada sosai Yace shikenan ga mom dinki"" saida tadan yakuna fuska kamar wacce taji anfadi abun kazanta tace bata mugaisa yace to tareda mikawa lubabatu wayar Damamaki take kallon wayar tamaida kallonta wajenshi tace wayene?? tasan labilace Amman kuma tundatake labila bata tabacewa abata wayaba shine takeson gazgata abunda taji Usman yace kinajifa sanda nakirah sunanta to labilace zakugaisa"" Tamika hannu takarbi wayar takara akunnenta batareda tace komaiba Labila takatsemata tunani tace mom kinyi mamakin jinnace abanike mugaisako??? Hmm bawani abubane kawaidai inason insanardake yarki tahardace hizifi arba in acikin littafi mai tsarkii za ayimasu walima Yanadakyau kema kisamu kizo walimar kozaki tuba kidaina abunda kikeyi kumakinemi gafaran dad dankuwa kina cutardashi nabarki lafiya Tanakaiwa nan takashe kiran"" lubabatu tayi murmushi tamikawa Usman wayarsa batace komaiba Amman aranta tana jinjiina maganar labila Usman yanisa yanamai kallonta yace waiku meyasa haryanzu bakwa barin wannan al adar taku waishikenan idan kanada darfari bazaka sakemasa fuskaba?? Saikanuna tamkarma bakasonsa alhalinkuma kanason sa wayezaihaifi dayace bayasonsa Amman abunda kuke nunawa yayan fari baidaceba hartakai sukansu basa sakinjiki daku"" lubabatu tasaukarda ajiyar zuciya tace to aihakan mukatashi mukaga anayi ai kunyace bawai rashin soyayyaba"" baki kawai yamere yacigaba da kallonsa Itama batakoma kansaba tundadai basurutun takeson yiba"" washe gari kuwa ya mata siyayya kaya masu kyau ya aiki driver yakaimata tareda kudi takara wajen hidima Tun anasauran sati daya walimar akasoma sanarwa kafafen yada labarai su labila ansha kyau anyi gyaran gashi da itah da sahiba anko sukayi komai nasu iri dayane"" hatta kunshi da akaimasu zanen iridayane Anagobe walimar labila agidansu sahiba takwana saboda batakarisa hardartaba"" sahiba sai dariya take mata waitafaye son wasane takaimata dukan wasa tagoce tana dariya "" labila tace wlh bawasa bane kinsan baiwa kowa da irin tasa tace hakane"" yauwa sahiba banfadamaki ba gobedai babana zaizo inaso zannuna makishi kugaisa tunda baizoba sannan Tace shikenan sahiba Amman kinsan wani abu??? Labila tace ah ah saikinfada"" tayi shiru daga bisani tace wlh tunsanda akacemaki saurah kwana biyu walimar nan gabana yaketa faduwa narasa dalilin faduwar gaban"" Labila takalleta saikuma takyalkyale da dariya tace Allah yasadai alkhairine"" mukam musha biki "" takalleta da harara tace dagafaduwar gaba kuma saikusha biki ?? Tobikin mene??? Labila tana linke kayansu tace kikasani ko wani kyakkyawa zakiyi gamodashi"" tace waini??? Haba sahiba ainayi kankanta dayin aure yanzu sainan gaba aikoke bazakiso nayi aure yanzuba Labila tace saboda me?? aini tuni nazaba miki miji kawaidai inajiran hukuncin Allah ne yazabamun abunda yafi akhairi nasankuwa kowaye nazabawa sahibata bazataki amincewaba Murmushi kawai tayi batasake cewa komaiba!! Harabar islamiyyar cike take makil damutane bakako hangen karshensu gabas dayamma hangu da dama dandazon dalibaine wadanda suka sauke dakuma masu harda Cen saman dandamali malaman makarantane""gefensu kuma wata babbar rumface shake take damanyan mutane yankasuwa suwagabanni harda sarkin kano yana cikin shigarsa ta alfarma"" gefensa fadawansane sukemasa fiffita gamnoni daga kasashe daban daban duka sun ziyarci wannan walimar domin taya daliban dakuma iyayensu Murnar wannan babban abudasu kasamu nahardace littafi mai tsarkii Bayan annatsu aka kirah amirar makarantar wato khadija Muhammad domin tabude taro da addua"" Wata karamar yarinya naga tataso cikin shigarta ta alfarma tanasanye dahijab harkasa fuskarta lullube take cikin likab kafarta tanasanye da safa shekarunta bazasu haurah goma sha shida ba" tana tafiyarta cikin natsuwa idanuwanta suna kasaa Takarasa inda malamin yake tadan gurfana takarbi lasifikar tasoma addua Cikin harshen larabcii gabadaya wajen kaji yayi tsitt bayan tagama bude taro da addua takoma mazauninta Usman gabadaya yarasa natsuwarsa saibinta yakeda kallo tunsanda aka kirah sunanta yaketa nanata sunan aransa Shikanshi tunsanda anasaura kwana hudu walimar yakejin matsanancin faduwar gaba"" saiyanzu dayaji muryanta yasakejin faduwar gaban tayawaitaa idanunsa suna kanta duk da akwai tazara maiyawa atsakaninsu Kusada itah watace zaune itama cikin shigar kamar ta khadija tsayinsu zaizo kusan dayasam hankalin Usman bayawajenda ake gabatarda dalibai tundaga matakin sauka har aka kai matakin harda Aisha✍🏼 ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠ Chapter 54 By Gentle Lady💃🏽 Akasoma kiran masu harda" tundaga mataki nafarko masu hizifi biyar har akakai kan masu hizifii arba in labila Usman itace wacce akasoma kirah Usman saiyanzu hankalinsa yadawo jikinsa jin ankirah gudan jininsa yasoma dube dube yaga ta inda zata bullo Idanuwansa sundauke daga gunda labilar take tacewa sahiba kitayani addua please tana dariya tace kije kawai zakiyi nasara insha Allah"" labila tawuce cikin takunta ahankali saidai yaji tasoma kira a Sosai yanatsu yana sauraren yarsa harta kammala akasomayi mata tambayoyi akan fikihu da kawa idi wasu hawayen dadine suka sauko akan idanuwansa yakaikaice yashafe yanamai sake godewa Allah daya nuna masa wannan ranar"" Bayan tagama akacigaba dakiran sauran har aka kai matakin hardar hizifi sittin akasoma kiransu dai bayan daya" karshe akakirah amerah wato khadija Muhammad tanacikin masu hardar hizifi sittin tunkafin tasoma karatu gabadaya wajen yakaure da kabbara!! tasoma karatun fatiha acikin daddan sautiii maimatukar sanyi dakuma kashe jiki""tana kammalawa tasoma karanto suratul bakarah gabadaya wajen yayi tsit Usman sai lunshe idonsa yakeyi saboda dadin karatun kowanne harafi tanabasa hakkinsa wajen gunna tafitarda gunna kowanne harafi tana fadinsa daidai"" harwata kasala tasaukar masa"" Yayi nisa wajen tunani hartagama akasoma yimata tambayoyi tana bada amsa daidai bayan takammala takoma mazauninta"" Gabadaya wajen akasake kaurewa da kabbara kowayasaurari karatun khadija dole yayi kwadayin inama ace yarsace wannan kokuma yayi kwadayin yasamu mata kamarta Usman yanadai dagacikin wadanda suka furta hakan azuciyarsu"" bayan ankammala akasoma rarraba kyauta dagukkan dalibai"" inda abangaren masu hardar hizifi sittin khadijace tazo tadaya tasamu kyauta maitarin yawa ciki kuwa harda kujerar makka"" sosai taburge kowa tayanda akabata kyautarta "" saitasoma kuka domin tunawa da mahaifiyarta inama tana raye taga yanda abunda tabari aduniya tazama Labilace tafito tajata zuwa wani aji tasoma rarrashinta tace haba sahiba wannan fa ranar farincikice menene abun kuka kuma keda zakinuna farincikinki cikin kuka tace sahiba mamana!! Labila tace Dan Allah kidaina kuka abun alfarine awajen mama ayaudin nan idan akanuna mata yanda kikazama bakuka zakiyiba sukarungume juna suna kuka saikuma akarasa Wanda zai rarrashi wani sunyi akalla mintuna ashirin awajen Amman basudako alamar daina kukan Yana tsaye yana kallonsu yarungume hannuwa saidai sukaji muryarsa yace kukan ya isah haka shima yana goge guntun hawayenda suka saukomasa kusan tare suka juya suna kallon kofa labila cikin muryar kuka tace kaiwaye??? Khadija takalleta cikin fara a tace sahiba Yayana nefa" ya muktar Bakitarike tareda murmushi""tace afuwan yayanmu tamaida kallonta wajen khadija tace Amman bakifadamun yazoba ai""" Takalleta tace nikaina bansan yazoba danmunyi waya jiya dashi dayakirah kawu cewa yayi baxaisamu zuwaba"" Takarasa wajensa cikin jindadi tafada jikinsa saikuma tasake fashewa dakuka""daya hannunsa yasaka yana bubbugar bayanta cikin tausayawa yana rarrashinta yace menene nakukan bagashi nazoba ??? Idankuma bazaki dainaba zantafi abuna baxansake zuwaba kinkuwa San aikinda yake gabana Amman nabarshi saboda kawai inga farincikinki"" tace nadaina Yayana karkatafi kabarni Labila tayi tsuru tana kallonsu cikin soda Kauna murmushine kwance akan fuskarta sunbala in matukar burgeta Sunanta taji anakirah aharabar waje khadija muhammad labila usman Hafsat m shareef "" yayi saurin jayeta daga jikinsa yace kije anakirah"" hawayenta takarasa sharewa tajuya wajen labila tareda murmushi tace mujeko sahiba Murmushi itama tamiyar mata tariko hannunta sukafita muktar yabisu da kallo sosai yanason kanwarsa dama wannan itace sahibar tata tanayawan bashi labarinta duk da baiga fuskartaba yanaji ajikinsa kyakkyawace Sunafita wajen yasake kaurewa da kabbara"" tare suka karasa wajenda aka kiraasu khadija takarbi lasifika tasoma yin addua sannan tasoma jawabin muhimmancin ilimin Islam cikin harshen larabci inda labila take fassarawa cikin harshen Hausa"" hafsat takeyi cikin harshen turanci daki daki sukebin komai Hakika nayarda Ilimi wani abune maidadi hakazalika maisanya nishadi azuciya"ilimi gishirine narayuwa"dukkan Wanda yakeda ilimin Islam bazaitaba tabewaba duniya da lahirah Allah yabamu ilimi mai amfani Bayan sunkammala khadija tayi Yar takaitacciyar nasiha gameda muhimmancin bin iyaye cikin harshen Hausa wadansu sunyi mamakin jinyanda take magana dahausa Dan Sam basuyi tsammanin tanajin hausaba Birrul walidaini"" wato biyayya ga iyaye "" Yakamata yan uwa musan mahimmancin iyaye arayuwarmu musaman uwa!! uwa!! uwa!!! Kasani komai kazama aduniya karkasake kawulakanta iyayenka babban abunda yake damun al ummarmu ayanzu dayawa mutane basusan darajar iyayensuba Baka daraja iyayenkaba toballantana kuma iyayen wani"" shinkokasan dukkan cigaba yana samuwane idan harkabi Allah da manzonsa sannan kuma kabi iyayenka"" wasu yayan babu ruwansu sudai kawai suyi abunda yake gabansu karkumanta wahalarda uwa takesha tunsanda kake cikinta ranarda zata haifeka wahala cikin wahala harkazo duniya tayi dawainiyar shayardakai sukabaka ilimi Amman dagakarshe saikayi tamkar bakasan dawainiyarda sukai dakaiba"" shinkayiwa kanka adalci kuwa??? Kokadauka basuda hakki akankane??? Kamar yanda akace matarka aljannarta tana karkashin kafarka haka kaima taka tana karkashin ta iyayenka inhar kasaba musu bazaka shiga aljannaba. Sukuma iyaye Susan tarbiyarda zasu baiwa yayansu domin suyi alfahari dasu"" abun alfaharinkane kaji ance wannan Wanda yacinye gasar musabaka aidan wanene bazakaso kaji ance ankama danka yana kanta daureba kokaji ance aidanka babban danfashine Ku kyautata atsakanin Yaya yenku Manzon Allah yanacewa awani hadisi"" وقال صلی الله ءليه وسلم ساووا بين أولادكم kusasanta "atsakanin yayanku a Awani hadisi manzon Allah yabacewa وقال صلى الله ءليه وسلم إن من حق الولد ءلى والده أن يعلمه الكتا به و أن يحسن اسمه و أن يزوجه إذا بلغ رواه النجار Yanadaga hakkinda yarataya akan iyaye bisaga yayansu ya karantardashi littafinshi ma ana alqur ani maigirma "" kokai zaka karantardashi kokuma kakaishi islamiyaya la ba asan"" '' ka kyautata sunansa"" sannan ka aurardashi idan yabalaga"" Aisha✍🏼 ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠ chapter 55 By Gentle Lady💃🏽 وقال صلى الله ءليه وسلم من بلي من ه‍ذه البنات بشيء فاحسن اليه‍ن کن له ستر من النار Wanda yakeda Yaya biyu mata ya kyautata agaresu ma ana ya tarbiyantardasu harsuka girma ya aurardasu zasu zame masa sutrah daga daga wuta""" Inakirah ga iyayena maza da mata dasu tsayu akan Yaya yensu kusan kalar tarbiyarda zakubaiwa yayanku domin duniya tayi alfahari dasu Kukasance kuna ciyarda matayenku abinci na halat domin samun Yaya nagari masu biyayya agareku sannan kusa ido akan yayanku abokansu makotanku yanda suke mu amala Musamman wannan zamanin damuke ciki wai uba zaiyi zina dayarsa Yaya. Yayi zina dakanwarsa makoci yayi zina da matar makocinsa da yayi zina da mahaifiyarsa wa iyazubillah waihartakai anayiwa kananun yara fyade kayiwa yarshekara biyar ko uku ko hudu fyade bisabillahi mezakaji??? Banda zalunci kuma dakai za ayiwa yarka ko kanwarka yazakaji??? wai wane irin lokacine mukeciki ayanzu babu shakka manzon Allah yayi gaskiya Duk ilimi ya bace acikin alumma barna tayawaita adoron kasa tobala ine zaiyita shigowa gashinan kuwa munagani Duk wannan tsadar rayuwar damuka samu kanmu aciki mune mukajawa kanmu"" kashe mutane sai yawaita yakeyi anmaida rayuwar mutane tamkar takiyashi kiyashima yafita daraja Lalacewar Yaya iyaye sunada hannu dumu dumu yaro tunyana karami ake koyardashi yanda zaibi Allah Amman wasu iyayen koda sunga yaro yanayin badaidaiba wani yayi magana saisuce kukyaleshi kuruciyace Wai kuruciya bayankuma ayanzune yadace kuginamasa komai tayanda zai zauna akansa Manzon Allah yanacewa awani hadisi"" هفزل غلم سغرن كنكسن بلهحر .وهفزل رحل بااد ميغبر كل كتبت ألل ماء kiyayewar yaro karami kamar rubutune bisa dutse kiyayewar babban mutum bayan yagirma kamar rubutune bisaga ruwa Idankukai rubutu akan dutse zai zaunane daram bazaitaba gogewaba sai idan zakusaka nakiya ne kufasa dutsen kodakuwa kunyi hakan za asamu wani gefen darubutun Amman bazaitaba goguwaba Amman kugwadayin rubutu akan ruwa kugani shinzai tsayakuwa???? Tokamar hakane idan yaro yagirma babu abunda zai iyah tsayawa akansa Hausawa sukance icce tunyana danyensa ake tankwasashi idankuwa yabushe bazai tankwasuba inharkuwa kamatsa saidai yakarye Tokamar hakane idankukaga yayanku sunayin abunda baidaceba kutsawatar masu kuma kuzaunardasu kununa masu illar yin hakan kusanardasu irin azabarda akeyiwa mai aikata hakan tozasuji tsoron aikatawa Kundarsa masu tsoron aransu dashikuma zasutashi""misali kamar yanda akecewa yara Karya haramunne maikarya Dan wutane Zakaji yara harsunayi dawaka idansukaji wani yayi karyaa"" ya Allah kashiryar mana da zuriyarmu Kaine maishiryarda Wanda kaso idan kashiryarda mutum babu mai iya batardashi idankuma mutum yabace babu mai iyah ganardashi gaskiya sai idan kaso Allah kakaremana yayanmu da jikokinmu yan uwanmu musulmai duka kabamu ilimi mai amfaninmu duniya da lahirah kadoramu akan tafarkin gaskiya"" kasadamu da rahamarka"" رب اغفرلي وتب ءلي إنك أنت التواب الغفور. سبحا نك الله‍م وبحمدك أشه‍د ان لاإله إلاأنت أستغرك وأتوب إليك Tamikawa malamin lasifikar"" gabadaya akakaure wajen da kabbara Cikin natsuwa suka karasacikin taron wajen muktar tatafi"" inda akarufe taro da addua"" akasoma watsewa saiyanzu labila taga dad inta"" yana nufosu"" da fara a afusarka"" Hajiya tace yan kaduna saukar yaushe??? Yace kafin afara nakaraso labila tagaidashi ya amsa yana tayata murna" Dukawa yayi yagaida hajiya ta amsa cikin sakin fuska yabawa Hafiz hannu suka gaisa yace kaga yarka ko banyi tsammanin haka takeda kokariba Hafiz yace hakane Yaya ai ina shirye shiryen turata saudiya tayi karatu acen inshaa Allah sai anyi alfari da itah Majeed yace uncle nikumafa??? Kansa yashafo yace sha kuruminka aihardakai za aje inajirane kaima kasauka kamar yanda tasauka saika miyarda hankali sosai idan kanaso katafiii Hajiya tace tomuwuce gida ko"" labila tace nidai hajiya kukarasa nizan jirah sahibane mutafi tare"" Usman yace wainikuwa wacece sahibar nan??? Kullum maganarki sahibadai sahibadai yaudaikam inaso naga wannan sahibar Tace zakaganta kuwa dad"" yace lallaikam inason ganinta dankam nalurah bakaramin so kike mataba Hajiya tace inama kasan haka kayanda kasiyomata cewa tai bazata sakasuba saboda bakasiyo biyuba da itah da sahiba saboda Hafiz yasaba komai zaisiyo dolensa yasiyo biyu idankuma bahakaba bazatayi amfani dashiba"" Yace um lallai naga alama tokutafi muje gidan gabadayansu suka karasa wajen motarda Hafiz yazoda itah"" Labila kam wajen sahiba takoma tacemata suwuce gida"" dayake bawani nisa dasubane tsakanin gidansu da islamiyya Amman akwai yartafiya Motar abokin muktar suka shiga zuwa gida"" anakaiwa gidan taja hannunta tace muje kigaisa da babana"" Juyawa tayi tace Yaya inazuwa yanzun zandawo yace to ba Matsala sukawuce cikin gidan gaban khadija sai yatsananta bugawa Zaune yake shikadai acikin falon wayace ahannunsa yana latsawa tunda sukayi ido biyu da ita tasanne kwayar idonta kasa wani abune takeji yanamata yawo ajiki tareda harbawar kirjinta Taresuka duka tace inawuni daddy wani sanyine yaji yaratsashi aransa yace ya salam badai khadija itace Kawar labilaba??? Labila takatsemasa tunani tahanyar cewa dad ga kawata sunanta khadija Amman yangidansu sunakiranta da safna saboda sunan mahaifiyartane Nikuma inakiranta sahiba dad inasonta fiye dayanda nakeson kaina itah marainiyace mamanta tarasu tana zaunene ahannun kawunta tareda yayanta Sannan takalli khadija tace sahiba ga babana""" abun alfaharina kuma maisharemun kukana"" yaudai kinga babana ko Khadija tasake dago kai karaf sukasakeyin ido hudu dasauri tamike jikinta yana karkarwa"" tace sahiba bari naduba wani Abu Tayi gaba Usman yabita dakallo hartashige dakin labila yasaukarda gajeruwar ajiyar zuciya labila tana kallonsa Da kuma yanayinda yashiga Yadawo dakallonsa wajen labila saiyaga shiitake kallo nantake yaji wata irin kunya takamashi"" murmushi labila tayi tace dad barinaje gurintaa Aisha✍🏼 ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠ Chapter 56 By Gentle Lady💃🏽 Kasace mata komai yayi saboda kunyarda yaji"" mikewa tayi kawai tana murmushi tawuce abunta"" Bangaren khadija kuwa tanashiga daki tafada akan gado tadafe saitin zuciyarta inda yake harbawa tamkar kirjinta ne zaifaso zuciyar tafito Tanacewa لاهولاولاقوت الابل لله kasa samun natsuwa tayi duk da jero adduarda takeyi bataji wani sauyiba azuciyarta "" tagumi tayi yayinda tashiga wata duniyar daban murmushi tasaki afili batasan sanda bakinta yafurta gaskiya kyakkyawane Daidai shigowar labila tace baban nawa?? Kunyace takama khadija tace nifa badawata manufa nafadaba ina nufin yanada kyau Ashe shikika biyo ba ummaba""" Nantake annurin fuskar labila yagushe"" khadija talurah dahakan tace meyafaru sahiba??? Kodai bakiji dadin abunda nafadabane??? Labila tace bakomai kawaidai naji raina yabacine!!! Tatari nunfashinta dakikaji na ambaci umma ko??? Waime yasaka kullum naketa jankunnenki akan muhimmancin umma agareki?? Tanisa kodayake tunda kinada itah araye bazaki gane mahimmancinta ba saikin rasata Labila tace sahiba kenan wlh dama nice ke dama tun wajen haihuwana tamutu"" khadija tayi saurin rufemata baki tace a uzubillahi Allahumma izna min hazal kalamiki"" kinkuwasan mekike fada??? Kinaso yayanki sucemaki hakan"" wasu hawayen takaici tashare tace inhar banzama nagartacciyar uwaba bazanga laifinsuba koda jifana sukai da dutse Khadija tadafata tace kome kikeji agameda ummah hakuri zakiyi itace dai mahaifiyarki kuma kinsan babu Wanda zai karkare hakan Labila tanisa tace babban takaicina kenan danashigo cikin tsatsonta inama ace babana ba itah ya auraba har aka haifeni Khadija tabata fuska tace sahiba waime yasakike hakane kin isah kisauya hukuncin Allah ne"" kisani kowa dakikagani aduniya bai isah yagoge kaddarar saba Ballanata ummah batada wata makusa kawaidai dankina yarfarine yasa batajanki ajikinta tokuma bakece kawai akayiwa hakanba kigaggauta Neman tuba awajen Allah Tashare hawayenta tana maineman yafiya awajen Allah astagfirullah wa atubu ilaihi"" aranta kuwa tana mamaki yanda take kasa sanarda wani damuwarta Khadija ce tajawo hannunta tafada saman gadon"" tace kiyi hakuri kinji sahibata wlh banason inaganin damuwa atare dake kwata kwata kasa samun sukuni nakeyi Labila tayi murmushi nadaina sahiba kinga ya muktar fa yana jiranki muje narakaki indawo wajen dad Tace to tareda mikewa "" aranta tanata addua Allah yasa bayacikin falon labila tanagaba tana binta baya Yana nan kamardai yanda sukabarshi Amman yadorah kafarsa daya akan dayaa sabanin dazun dayake danna waya yanzu idanuwansa kyam sunakan kofardasu labila suka shiga Suna fitowa yatada kansa zuwa fuskarta take idanuwansu suka sarke cikin najuna dasauri khadija tasaki likaf yakarasa rufemata yan idanuwanta dama sune kawai abude Wani iri yaji aransa kardai yarinyar nan tagano itah nake kallo?? Muryanta yaji tanacewa dady sai anjima""" yadago ahankali yakuramata ido saikuma yasaki murmushi yace to Khady kigaida gida" taresuka fita da labila yarakasu da ido Khadija kafarta har sassarfa takeyi"" sunafita Usman yadafe kansa yace ya salam meyake shirin faruwa dani wannan wane irin abun kunyane zuciyata takeson kaini gareshi kawar yata!! Yayi saurin kawarda tunanin aransa tunkafin yasamu matsuguni Wayarsa yadauko yakunna kira a yadorah akan kunnensa yadan kishingida saman kujerar babu jimawa barci yadaukeshi awajen Hajiya yaji tana tashinsa yatashi yayi sallar la asar gashicen anyi kirah mikewa yayi tareda mika yawuce zuwa dakinsa dayake gidan Yana nan tsaf dashi tamkar akwai mutum aciki toilet yashiga yawatsa ruwa sannan yadauro alwala yawuce masallaci acen yahadu da Hafiz Bayan sundawo ahanya yake masa maganar yaushe zaikoma america yace wani sati ainakusa gamawa inhuta yawon nan basonsa nakeyiba Usman yace Allah yataimaka aini namatsu kagama in hannan tamaku dukiyarku"" Hafiz yace habadai Yaya niba fa kasuwanci zanyiba aikin gamnati zanyi Kawaidai kacigaba dakula dasu Yana dariya yayi maganar Usman yace naki wayon nauyi yayimun yawa akaina bazaku ragemunba"" Hafiz yace aigirman Kane""Kaine fa babanmu dole kakarbi girman"" Usman yace naji waikai yamaganar auren inata zuba ido naji tsit karfa yarka tarigaka aure??? Kakuwasan dakaji kunya'' Hafiz yasosa kai yace aini karamin ubane bazanji kunyaba tunda Ban isah aureba"" Usman yaharareshi yace ahakan??? Tokodai kafitarda mata ko inhadaka da Abu mai kuli kuli da awara"" baki Hafiz yarike yace abun haryakai cen tokwantarda hankalinka dazaran nadawo zakaji komai Usman yace sauran watanawa??? Hafiz yace bakwai koyanzu walimar labila tadawo dani danbanaso ayi bana nan" Usman yace shikenan munadai zuba ido daidai sunkai kofar gidansu sukashiga tare sunafira suna raha hajiya bakaramin dadi takejiba idan taga yayanta cikin farinciki Saman kujerah suka zube labila tadauko masu abinci sukaci sukahau firah sai shida saurah Usman yayi haramar tafiya harbakin mota suka rakashi yawuce yana daga masu hannu Labila batakoma gidan sahiba ba saboda hankalinta yanakan yayanta shima washe gari tunda safe zaikoma"" Agogon Nigeria yabuga karfe biyu nadare alokacinda nasan kowa yayi nisa cikin barcinsa saikuma masu ibadar dare. Bakajin motsin komai saikukan karnuka dasuke cikin layin Inkadauke Usman dayake tsaye yakai gwauro yakai mari tunsanda yabaro kano yakasa samun sukuni cikin ransa"" komai yakeyi fuskarta yakegani sanye cikin nikaf haryana ayyana suffarta yanda zata kasance Gabadaya ta dabai bayemasa zuciya dakuma tunaninsa hatta abinci idan zaici fuskarta yake hangowa akan plate wanan wace irin makauniyar soyayya ce???? Kawar labila yafurta ahankali komawa yayi saman gadon yazauna yadafe kansa wanda yayimasa nauyi Kai bazaitaba yuyuwaba wlh tunwuri dama kindaina son abunda bazakitaba samun saba dawanne ido zan kalli labila ince inason kawarta ??? Taya zata kalli maganata?? Yakamata inhana zuciyata afkawa inda baichanchanci yazama muhallinaba "" wata zuciya tace masa taya hakan zai yiyu kokamanta soyayya batayin shawara dakowa Yayinda zatashigeka batadubà matsayi kochanchantar Abu"" yace idankuwa hakane gaskiya bataimun adalciba saboda abun nan bazaitaba yiyuwaba"" Wata zuciya tacemasa yiyuwa kai saidai inhar bakace kanasontaba koda kaki fada Dole sai zuciyarka ta tilas taka Yace wlh karyane wannan abun kunyar badanibà ganin abun yanason haifarmasa da damuwa yayisaurin kawarda tunanin abun yafaskara tashi yayi yadauro alwala yasoma nafila yanarokoñ Allah yaciremasa sonta tunkafin yayinisa Saikusan asuba yakwanta Amman abun mamaki maimakon yaga sauyi aransa saiyaji kamar ansake linka sonnata sau ashirin acikin zuciyarsa Aisha✍🏼 ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠ chapter 57 By Gentle Lady💃🏽 Har akayi kiran asalatu idonsa biyu bairuntsaba"" tashi yayi yasake dauro alwala yafita yatada lubabatu sannan yakarasa sauka kasa yasoma tashin yan aikin gidan kamardai yanda yasaba Saida sukai alwala sukawuce masallaci baidawo ba saida haske yagama mamaye gari cikin masallacin ma zaune kawai yake tamkar mutum mutumi tundayake baitabajin soyayya irin hakaba Waidama Ashe haka soyake??? Lallai Wanda baisan soba shine zai karyatashi baitaba tunanin hakan akejiba gameda abunda zuciya takeso tomeyasa banajin hakan lokacinda nahadu da lubabatu??? Kodai itakanta soyyyar matsayi matsayine da itah nasan Na auretane Dan inasonta towacce irin soyayya??? Kawaidai inajinta cikin raina yanda baxan iyah rabuwa da itah ba Sauran matanda na aurah fa??? Sume yasa banajin haka atattare dasu??? Suma tasu kalar soyayyar dabantake Khadija ce kawai lokaci daya soyyyarta tashiga harcikin barko dakuma jinin jikina"" tomeyasa hakan??? Saboda kanasonta"" !! Tomeyasa nakesonta alhalin kofuskarta banganiba ??? Saboda tarbiyarta to ai itama lubabatu tanada tarbiya meyasa banajin sonta kamar wannan ??? Wannan kuma daga Allah ne Haka yayita yiwakansa tambayoyi kuma yanabawa kansa amsar tambayarsa haryabaro masallacin kwana biyu tsakani yakasa gane kansa abinci kansa yarage ci Zaune yake office dinsa yana tunani yakamata insanarda labila halinda nakeciki nasan bazata zargeniba saboda tasan banine nasakawa kainaba"" kai anya zan iyah kuwa??? Tomezaihana kadai tsaya kallon ruwa kwado yayimaka kafa kawai kasanarda itah zata fuskanceka dawannan shawarar yayarda yadauko wayar yakamo lanbar Sannan yasoma jujjuya wayar Yayi tsayin mintuna ashirin sannan yakirah"" tanafara ringing yaji gabansa yafadii rasss"" tayita ringing harta katse ba adaukaba yasake kirah hartakatse bata dagaba Khadija tana kwance adakin wayar tasoma ruri harzata daga taga sunan wanda yakirah dadyna gabantane yabada rasss tadafe kirjinta tanamairufe idonta Waimenene hakan kikeyi babananefa"" taja tsakii hartakai hannu tadauka kuma takasa saida yayi kiran saubiyu gana uku tadauka Jikinta yanadan rawa cikin siririyar muryanta tace Assalamu Alaikum daya bangaren wani irin sanyine yaratsa zuciyar usman haryasaukarda gajeruwar ajiyar zuciya Yace Amin wa Alaikumus salam" Wani yanayi khadija tasamu kanta aciki jin muryarsa yasaukar mata da kasala cikin sassarfar murya tace dady ina kwana"" yace lafiya qalau kina lafiya tace umm sannan tace batanan taje gida tadawo batajirah mezaiceba taka she kiran Tace wai tareda murmushi tanadafe da kirjinta dayake harbawa"" Yanajin taka she yajiwani iri cikin ransa Sam baijidadin hakanba"" yaso koda muryantane yaji yanatsaka da tunani saigakirah yashigo Dasauri yadauka atsammaninsa itace tasake kirah yanadauka yaji muryan labila bahakan yasoba cikin sanyin murya ya amsa gaisuwarta tace dad tundakazo bakasake kiranaba Yadan shafo kansa yace tubanake aikine yayimun yawa wlh "" tace shikenan yace yasu hajiyafa??? Tace qalau munga sako dani dasahiba mungode Yadan murmusa bakomai tayidanjin dad akwai matsalane??? Yace ah yayi saurin cewa sorry ah ah babuwata damuwa kinga wani abune??? Tace dad aibahakan nasabajin muryankaba indai akwai damuwa kasanardani please"" yace bakomai dama nakirakiine naji idan kina lafiya Tanisa qalau nake dad yace tosai anjima"" tace inasonka dad cikin sanyin murya yace nimahaka yakashe kiran yanamai runtse idanuwansa why why meyasa nakasa sanarda itah??? Bayankuma tatambayeni damuwata yayi wulgi dawayar yadafe kansa wani irin suracine yake fitowa tajikin zuciyarsa yanafita ta hancinsa tamkar suracin tafashasshen ruwan zafii Labila tsuru tayi tana kallon wayar"" khadija tace yadai sahiba???? Ajiyar zuciya tasaukar tace bakomai tareda zaunawa saman gadon""" Abu wasa wasa kullum saiyakirata kamar yasanarda itah saikuma yafasa itah tagano manufarsa Dantun ranarda yazo walima taga kallonda yakeyiwa khadija kawaidai yana jinjina sanarda itane amatsayinta nayarsa itakuma taraya aranta inhar bashine yafurtaba bazata taba nuna taganoshiba sai idan yatunkareta da maganar Yau yakasance weekend ne karfe takwas nasafe Usman yakama hanyar kano yaukam zaisanarda labila abunda ke zuciyarshi saidai koma kunyar ne yajita danyagaji da ajiyar abunda yafi karfin zuciyarshi Bangaredaya kuma yanason ganin khadija koda muryantane yaji zaiji sanyi "" koda yakarasa gidan hajiya bata nan"" dama kuma Hafiz Yakoma"" bayan yayi pkng suka gaisa damaigadi yake sanardashi yace bakowa gidan kenan??? Yace ah ah yar dady tana nan"" kamar yacemasa tareda kawarta saikuma yashare yawuce cikin gidan tanajiyo sallamarsa tafito dagudu tanamasa oyoyo Yace labila waiyaushe zaki girmane aiyanzu kinwuce wannan saidai majeed "" baki taturo tace ah ah banwuceba sai anhaifamun Kanwa sannan Murmushi yayi yanasamun waje yaxauna yacire hularsa yana fiffita kaiyaufa akwai zafi babu wutane??? Tace ah yanzun nan tadauke bari inkawo maka ruwa tayi maganar tana wucewa ruwa tadauko masa tareda cup tadauro akan wani karamin faranti maikyau taduka ta ajemasa tanayimasa ya hanya Yace alhamdulillah ruwan tazuba masa Tamika masa yakarba yanasha wani sanyine yake ratsashi saida yashanye duka tace akarane dad??? Yace kara Amman kadan Tasake Karamasa yashanye sannan yasaukarda ajiyar zuciya yace Alhamdulillah nagode"" inakuma hajiya taje baba maigadi yacemun tafita??? Tace ah wlh gidan wata kawarta akayi rasuwa shine tatafi gaisuwa"" yace ayya wayarasu mace ko namiji"" tace wlh bansaniba nima Yace to Allah yajikan Wanda yarasu tace Ameen" Amman meyasa bakibita kuntafi tareba""??? Tace dad kusa da islamiyar munefa kuma zasuga banzoba saitace induba gida sahiba ma tatafi tundaxu Shiru yayi baisake cewa komaiba gashi yanason magana Amman yakasa....... Aisha✍🏼 ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠ chapter 59 By Gentle Lady💃🏽 Yace nidai hajiya natafi"" sukayimasa Allah yakiyaye yawuce cikin farinciki gabadaya jiyake tamkar anyaye masa wani katon dutse daya taushe zuciyarsa fatansa kawai Allah yasa khadija zata ameence Dawan nan tunanin yakarasa gida"" lubabatu tana zaune cikin falon kasa tana kallo yanashigowa tabishi dakallon mamaki Kusa da itah yazauna yace yakina kallona bazakimun kosannu dazuwaba"" baki tatabe tace aibansan inda katafiba kaida bakafita koda kofar gidane idanhar ranar weekend ne Amman yaunaga bakon al amari Yanisa yanashafar kansa yace kano natafi"" takalleshi dahanzari tace incekodai lafiya??? Yace qalau natafi ganinsune kawai yaunatashi dason ganin Ya'yana Har abada baida niyar boyemata Amman yasamu kansa dakin sanarda itah dalilinsa nazuwa kano tundasafe dankoda yabarta bata tashi barciba shima saman hanya yasha lemu Tace wlh harkasa gabana yafadi nadauka wani abune yafaru"" yace bakomai wlh hamma yayi yana Shafa cikinsa yace akwai ragowar abinci yunwa nakeji Tace babu iyah cikina kawai nace agirka kuma nacinye inda kafito bakaci abinci bane??? Shiru yayi baice komaiba "" tace sai idan kanaso nasake sakawa adafa maka wani"' yace shikenan barshi kawai nahakurah inci dadare"" Baijirah jin mezatace ba yamike yahaura sama tabishi damugun kallo"" sosai tanason tarika juya Usman tamkar dancikinta Amman tarasa gane dalilinda yasaka duk aikinda akaimasa baicika tasiri akansaba Wanda akayi cikin kwalbane kawai yakeyin aiki akansa kumashi zafin zuciya kawai yake sakashi idankuma takulle barta mutane har itah kanta bata tsirah da fushinsa Abokanta duka suna juya mazajensu son ransu duk da batanemi komai tarasaba Amman tanason harta wanki shine zaiyi mata dagyaran daki Tanajin tsoron sakashi tunda tasan yanada zuciya zata iyah sakashi yace bazaiyiba girmantama dayake gani yadaina gani kuma batason kowa yarika zargin wani Abu Usman tunda yahau saman baisaukoba saida yaji kiran sallar la asar yasake watsa ruwa yadauro alwala yasauko tana nan inda yabarta yawuce abunshi batareda yacemata komaiba Itama batadamuba Dan hankalinta yanakan TV datake kallo"" Kwance take dakin khadija itakuma tanazaune tana yankan kumba"" labila tace sahiba dama magana nakeso muyi dake"".. Tana yankan kumbar ta daina inajinki"" labila tanisa tace gameda alkawarinda mukaiwa juna yaudai inason nafurta maki sunan mijinda nazaba maki Khadija tayi kasake tana kallonta sannan tanisa tace sahiba atsarina inasone muyi aure tare kinaganin baiyi sauriba idan kika zabamun miji ayanzu Labila tatashi zaune tace nidai awajena baiyiba kuma nafison ayikomai dawuri"" Saidai idan zakiki zabinane Khadija tace habadai Nina isah naki abunda kikazabamun nasan har abada bazaki zabamun abunda zaicutardaniba"" Nayarda kowaye zansoshi sahiba idan harkedai yayi maki bamasai kintsaya Neman yardataba kawai kicemasa Na amince Labila tasaki fara a tace bahaka zamuyi dakeba inasone kifadi ra ayinki"" khadija tace inhar yayi maki wlh yayimun"" karkidamu Labila tace shikenan Amman akwai bukatar kusamu lokaci domin kugana kafin nan zansanardashi yaturo iyayensa atsaida magana domin cikin kankanin lokaci za ayi bikin"" khadija tace haba sahiba karatunfa!?? Karkidamu da karatu zakicigaba agidanki"" tace shikenan Allah yatabbatar mana da alkhairi labila tace Ameen tarungumeta cikin jindadi Bayan kwana uku kamardai yanda sukayi dashi saigashi yakirata tana falo tanayiwa hajiya tausa tamike dasauri tayi hanyar dakinta Hajiya tabita da kallo tana girgiza kai labila waisai yaushene zatayi hankali"" Allah yakyauta Tanashiga dakin tadauka tareda sallama ya amsa sallamar taredacewa lafiyadai naji shiru kodai kinmantane??? Nayita jiran kiranki gashi har dare yayi"" tace sorry dad wlh mantawa nayine""" idanuwa yakwalo aransa yace umm lallai bakisan abunda dadynki yakeji gameda itaba aida bazaki mantaba Takatsemasa tunaninsa tahanyar cewa ta amince""" baki yawashe yace dagaske??? Tace sosai ma yace Amman tasan nine tayarda dawuri haka??? Tanisa ah ah batasaniba Sai murnarsa takoma ciki yace mekikayi haka??? Taya zan aureta alhalin bakisanarda itah gaskiyar kowaye niba Tace naso fadamata saitace koma waye inhar niyayimun tobasaina nemi yardar taba"" tayarda"" tasan bazantaba zabamata abunda zaicutarda itaba Yayi shiru daga bisani yace ninasan bazata yardaba"" labila tace maisaukine dad yanzudai inaso kazo kasamu kawunta"" idan kungama magana"" saikazo danka ganta idan kaganta taganka komenene ninasan yanda zanyi Amman fa akwai sharadi bayan amincewarta"" yanisa wanne irin sharadi kuma labila??? Tace awajena maisaukine bansaniba kodai awajenka dakuma matarka!! Dif yayi shine illarfa kaso karamar yarinya kuma abokiyar yarsa yanisa shikenan kifadamun sharadin" tace bayanzu ba dad sai idan maganar ta tabbata yace shikenan Sukai sallama yadade yana nazarin kalaman labila daga bisani yadaga kafadarsa alamar baidamuba kowanne sharadine zai yarda dashi matukar zaisamu hadinkan Khadija dawan nan tunanin yawuni Bayan kwana biyu dazancen yaje kano hajiya yasamu yalabarta mata komai"" shiru tayi nawadansu lokutta sannan takalleshi tace anya khadija zatayarda idanhar tasan labila Kaine zabinda taimata??? Yanisa nikaina bansan yazata kayaba Amman banada mafita hajiya tunda kikaga harnayiwa labila magana kinsan abun nan ba karami bane Kece mahaifiyata nasan bazakiso abunda zaitaba lafiyataba wlh inacikin damuwa sosai abun yana Neman taba lafiyar jikina likita yacemun nadaina shan maganie nayi aure bansanarda ke bane kawai tunsanda kikaga inata aure Amman matanne duka kinga irin yanda suke kasancewa hardanacire son aure araina nabarwa Allah komai idan yazama shine ajalina Allah yagafartamun saigashi kwatsam naga wannan khadijar gabadaya narasa natsuwata"!!! Tanisa shikenan bari zanyi maka kwatancen shagonsa danbaicika zama agidaba kafara tuntubarsa dazancen kanemi izinin ganinta idan hartaganka kuma tayarda zata aureka komai zaizo cikin saukiii yace shikenan Tayi masa kwatance shagonsa akasuwa Yakuma sameshi yabashi hannu suka gaisa Ashe shima yasanshi"" Usman nekawai baiwayeshiba"" Aisha✍🏼 ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠ Chapter 58 By Gentle Lady💃🏽 Saiya kalleta kamar yayi magana saikuma yakasa itakuwa tana kallace dashi ganin yayi shiru tamike tace dad nikam bari nadan kwanta"" tayi maganar hartasoma tafiya Yace amm dawo labila magana zamuyi""" tace to tareda juyowa tazauna kasa tana fuskantarshi saikuma yayi shiru Yacije lebonsa nakasa yanasake jinjina nauyin maganar"" tace yadai daddy??? Yadan nisa yace bakomai tashi kije kikwanta Murmushi tayi maidan sauti tace dad kadaina boye abunda yake zuciyarka hakan babbar illace atareda zuciyar Komai nene kasanardani mana zanfuskanceka amatsayina nayarka banason damuwarka kokadan Kaine kawai kasan damuwana yanda zanfadamaka Abu bana iyah sanarda mahaifiyata Kadaure kasanardani wlh batunyauba nalurah kanacikin damuwa kullum kakirah ni dankasanardani saikuma kafasa Nifa yarkace menene bazaka fadamunba kaima kasani zanbaka goyon baya Dari bisa Dari idankuma abunda zanbada shawarane saina baka daidai sanina"" Yanisa yana kallonta yace hakane labila Amman gaskiya inajin nauyin fadamaki bukatata dankuwa tanada matukar nauyi. Tayimun nauyi abakina hakazalika zuciyata takasa daukarta inaganin kamar bankyautaba kuma abun kunyane Nayi nayi incire abun azuciyata Amman yagagara fita"" tanisa bakomai dad inhar fadinsa shine zaisaka zuciyarka nishadi kasanardani please Shiru yasakeyi nawadansu dakiku sannan yace labila akan kawarkine khadija tunranarda naji tana karatu amakaran tarku wajen walima haka kurum naji taburgeni Banyi tunanin kawarki bace saida kika nunamun itah sainayita kokarin incireta araina amman abun yafaskara Amman karki zargeni da wani Abu please Nasan abune maiwahalama tayarda ta aureni dannayimata tsufa"" dariyace takwacewa labila wacce tasaka Usman darawa tunfuskarsa nanuna alamar damuwa sanda yake maganar Saida tayi mai isarta tace haba dai dad akan yar wanann maganar dakake cewa kayimata tsufa ai wlh dad babu Wanda zaiganka yace kahaifi kamata"" Saidai kuma hanzari baguduba"" cikin sauri yace menene??? Tace sahibata tuni tayi mijin aure!! Wani kululu yaji yatokaremasa akahon zuci yayita maza yace shikenan dama haka Allah yakaddara Amman kibar maganar nan dagani saike saikuma Allah dayake kallonmu banaso tasan wannan batun kartadaina ganin girmana Labila tace harkasaki dawuri haka dady bayan kashiga kaima agwabza dakai"" yayi murmushin yake yace aikinsan bakyau Neman aure cikin aure Tace hakane tobaka tambayeni sunan Wanda zata auraba??? Yakishingida saman kujerah zuciyarsa nayimasa zugi yace menene amfanin jinsunan labila kawai kibar maganar kamar adole yake maganar Dan idanuwansa harsun sauya kala"" Marairaice murya tayi tace dad sahibar tawa??? Yace yihakuri towaye??? Tamurmusa sunanku daya ai Yace masha Allah inatayashi murna"" tace mungode kumafa akaduna yake zama unguwarku dayama Yalurah abunnata na ba ane yace kinsan Allah banason shashanci dariya tayi tace dagaskefa dad yanzun hakama munataredashi afalon nan Dasauri Usman yadago yanakarewa falon kallo baiga komaiba yamaida kallonsa wajenta yace waikina nufin ni??? Murmushine akan fuskarta tagyada kanta alamar ah Wani farinciki marar misaltuwa yamamaye masa zuciya bakinsa yaki rufuwa saboda tsananin murna tace nasan kayi mamaki danacekaine mijinta Tunbayauba nakeyimaka kwadayin samunta inada yakinin zakasamu abunda kakeso awajenta komenene dad tunda nahadu da sahiba wlh bantabajin tayi koda musayar yawu dawaniba Tanada hakuri gakuma addini bashakka zata tarbiyantarda yayanka kowanne uba anaso yasamarwa yayansa uwa tagari banada kokonto akan sahiba Nikaina dakaganni Allah yahadani da itah domin sanin halinda nakeciki Wanda babuwandà yasanshi sai Allah Munyi alkawari atsakaniñmu kowacce acikinmu daya zata zabamata miji tun alokacin nazabarwa sahiba kai kamar yanda nasanka haka itama Nasan zatayi alfahari dakai anan gaba kamar yanda kaima zakayi kumanasan baxata tabakin zabinda naimataba dukda sainayi dakyar kafin ta aminta idanhartaji nace zabinda naimata Kaine Tanisa tana kallonsa kabani kwana uku komainene zankiraka insanardàkai yanisa bakomai Amman idan batayardaba karki tilas tata akan abunda bataso dannima bazanji dadiba Tace in Allah yayarda zata amince"" yace to Allah yayardà labila yanaduba agogo yace bari nadanfità kafin hajiya tadawo Ammanfa karki manta da maganar please"" tace bazan mantaba dad tanarufe bakinta hajiya nayin sallama damamaki tace kai wanga saukar y aushe??? Labila tace bakijima dafitaba yashigo"" tace aidanasani danayi zamana tunanin nayi nakatsemaki makaranta shiyasama nadawo dawuri Usman yagaida itah ta amsa tana tambayarsa lubabatu"" yace qalau take hajiiya "" tace madallah saikitashi kishirya kiwuce makaranta Dan nakai majeed dagacen Taturo baki wlh hajiya nayi lattifa kafinma nakai antashi" Usman yace kishirya nakaiki daganan sai inwuce inda zanje Tace dad ankusa tashifa wlh danaje rikeni malam zaiyi sai azahar"" hajiya tace tosaiki zauna abokan karatunki saizu tsere maki "" Tace ai sahiba zata fadamun idan tadawo damakuma nawucesu dasura uku tunda inayi agida tayi maganar tana dariya murmushi Usman yayi yace nidai hajiya barinaje nadawo sainawuce Tace kaikuwa mekazoyi kano kanacikin aiki??? Murmushi yayi yadan Sosa kansa yace kawaidai nazo ingaishekune Tace kakyauta kuwa Allah yabada ladar zumunci yace Ameen tareda mikewa yadauki key dinsa yafita"" Saikusan azahar yadawo yaci abinci yawuce bayan yasake jaddadawa labila kartamanta"" tace bazata mantaba Hajiya tace waimenene aketa kumuiniya ba aso inji??? Usman yana dariya yace bakomai hajiya Baki tatabe tace komadai menene inazaune za afadamun indai wannan ce maishegen surutun tsiya"" kamar suda"" majeed ya kyalkyace da dariya yace Anty tazama suda hajiya dama aku kikacemata Labila tamaka masa harara"" tace zanbugeka majeed wasa nakeyi dakai??? Jikin hajiya yashige yace aihajiya bazata bari adakeniba"" Usman yana dariya yace saidai idan bakayi laifinba"" hajiya tace kodayayi laifi babu maidakarmun maigida inakallo"" majeed yacee yeee hajiya tanasona gabadaya sukasa dariya Aisha✍🏼 ☠ *HATSABIBIN BOKA!!!*☠ Chapter 60 By Gentle Lady💃🏽 Yace yanzun kazone??? Usman yace ah wlh .to ansamesu lfy ko???.. Yace cikin godiyar Allah""" to masha Allah ""Allah yakara mana lafiya Usman yace Ameen"" saikuma shiru yabiyo baya yalura akwai magana abakinsa yace Alhaji Usman mukarasa ciki ko babu musu yamike shikuma yashige gaba yanabiye dashi Dayake shagon babbane akwai kujeru biyu aciki yanuna masa bisimillah zauna taresuka zauna yasake bashi hannu suka gaisa""" Yace banyi mamakin ganinkaba nadauka wani kaya kazokasiya saikuma nalurah akwai magana abakinka"" Usman yasanne kansa yace hakane malam"" dama akan yarwajenkane "" tunranarda nazo walimar su labila naganta amakaranta naji takwantamun araina Banyi tunanin Kawar labila bace saida nagansu gida tare"" tun alokacin naso cireta araina"" saikuma abun yafaskara Kuma inajin nauyin nasanarda itah shine danasanarda labila tasanarda itah tace ta amince Amman kuma bata fadamata ainahin waye yakesontaba Shine Nazo wajenka Neman izini inaso inda hali ingana da itah banaso intilas tamata idanhar batasona karsai magana tayi nisa yazama nacutarda itah Danasanarda hajiya shine taturoni nan nayi tambaya har akanunamun shagonka"" inafatar ba aimata mijiba daga wurinku dagaske nake bawai wasa nazoyiba auren ta zanyi inda halima banaso adau tsawon lokaci yakai karshen maganar yana kallonsa Malam garba yanisa yace to Alhamdulillah naji dadin jin wannan maganar Amman wani hanzari baguduba gaskiya banine mahaifin yarinyar nanba"" asali uba muka hada da mahaifiyarta Mahaifinta Dan yolane sunrabu da mahaifiyarta tuntana ciki wata uku"" tazo tareda yayanta muktar anan garin dama nan ne tushenta"" ranar da tahaifeta aranar tarasu ko waigowa batayi taga yarba yayanta shiyayi rainonta hartagirma duk damaidakina tana kulada itah sosai bayason yayi nesa da itah Yanzun yana america wajen karatu ni awajena babu damuwa kafara ganawa dayarinyar idanhar ta aminta zankirah yayanta insanardashi saikasamu kashirya muje yola tare dakai duk daharyanzu babanta baitaba waiwayarmuba kodai yanedai muzamu nemishi Usman yace hakan yanada kyau Allah yajikanta"" yace Ameen daganan sukadan taba firah yayimasa sallama yakoma gidan yasanarda hajiya yace tafadawa labila zaidawo jibi yayimata sallama yatafi Ranarda takama zaizo takai khadija akayimata lalli akagyara mata kai tashirya masa abinci mairai dalafiya"" gidansu khadija suka karbi mabudin dakin ya muktar suka gyarashi suka kunna turaren wuta"" Dakinsai fitarda sihir taccen kamshi yakeyi"" da khadija taiwanka labilace tayimata kwalliya Dan itah bamaiyawan kwalliya bace Bayan tagama kimtsawa labila takalleta tundaga sama harkasa aranta tace dady hakika kayi dacen mata wacce zata share maka hawayenka Dakuma tatunoda gidanda zataturah kawarta saikuma tarungumeta tafashe dakuka"" bataso tarasa kawarta haka zalika tanason ganin karshen bokan mamarta kuma tasan babu wacce zata iyah tunkararsu sai khadija domin itace ta chanchanta Khadija tace lafiya sahiba idan bakyason abun nan karfa afara hankalina bazai kwantaba idan inaganinki cikin damuwa Labila tayi saurin share hawayenta tace karkidamu sahiba bawani abubane yasakani kuka ganin wannan kyanda kikayine kamarwata sarauniya Harara tayimata cikin wasa tace aikinfini kyau sahiba kawaidai bakyaganin nakine kina hango nawa"" zatayi magana kirah yashigo wayar labila Tadauka cikin fara a tayi sallama daya ban garen aka amsa tace harka iso??? Yace ah tace ok ganinan zuwa takashe kiran tana kaidubanta wajen khadija wacce takuramata ido bugun kirjinta harwaje kanajinsa Murmushi tasakarmata tace yadai sahiba??? Tasanne kanta kasa tanawasa dayan yatsunta tace wlh gabana faduwa yakeyi Kamar kirjina zaiballe"" labila tace please kisaki ranki nasan zaiyimaki kyakkyawane sosaifa barinakaishi dakin nadawo Tayi maganar tanaridar mayafinta tayafa tafita"" innah tana tsakar gida tacemata innah bakon ya iso"" tace to gashi bangama dama furarba barinayi sauri tace to tawuce Yanacikin motarsa yanaganin tafito yafito yana tunkarota da murmushi akan fuskarsa"" Tace dad inawuni"" yace lafiya qalau yagidan Tace qalau mukarasa ciki sainakirata ko"" yace to bisimillah"" tana gaba yanabinta abaya tabude masa dakin yashiga yazauna sannan tafita tayita jidomasa kayanda suka hadamasa takaimasa Shidai yakagara yayi ido biyu da khadija kamaryayi magana saikuma yadake kartace yafaye zumudi tazuba masa ruwa sannan tafita khadija takoma tamkar mutum mutumi duk jikinta yamutu labila tadauko hijab tasakamata"" Tariko hannunta sukafita haryanzu kirjinta harbawa yakeyi bakin dakin labila tatsaya tace kishiga inazuwa"" Khadija tamake kafada tace saidai mushiga tare"" labila ta kwalalo ido tace gaskiya bazai yiyuba haba"" Khadija tace tosaidai mukoma Amman kinsan bazan kebe dawani namijiba alhalin ba muharramina bane Tace kinyi gaskiya tokishiga dazaran kungaisa wlh zanshigo tace kintabbata??? Tace ah saiki tangale kofar idan kikashiga tace shikenan Labila tawuce tadade tsaye bakin kofar kafin tadaure tareda addu oi abakinta tasamu damar shiga dakin tareda sallama Wani sansanyar kamshin turarensa yadaki hancinta idonta yana kallon kasa cen nesa dashi taduka muryansa maisanyi taji taratsa dodon kunnenta wa alaikumus salam"" Gabantane yasake fadii talumshe idonta tabude aranta tace sak muryan dad"" murya kasa kasa tacemasa inawuni Idanuwansa suna kanta yace lafiya qalau Khady yagidan yakaratu"" wannan karon kam tunaninta yafara gagararta ahankali tadago kanta saicikin idonsa Zumbur tamike tadafe kirjinta tace dady dama Kaine??? Yanda take magana kasan tanacikin matsanancin tashin hankali gakuma bugun kirjinta ya tsananta Lallausan murmushi yasakar mata yace nine kinji mamakine khadija"" hawayenda suke akan fuskarta suka karasa gangarowa tace dad menene hakan?? labila dasaninta ta aikata hakan??? Yasakeyin murmushi yace balaifin labila bane nine nafara samunta da maganar"" cikin muryar kuka tace nashiga uku ni khadija menene sahiba ta aikata haka bazai yiyuba Kafin Usman yayi magana tuni khadija taruga tafita dakin tana kuka kamar ranta zaifita usman yatashi tsaye yana kiranta ina kojuyowa batayiba yadunkule hannunsa yanaushi iska Lebonsa nakasa yacije adayanaji kamar zai iyah hakurah da khadija Amman ganinda yamata ayanzu babu nikab yasake haukatoda soyayyarta ya Allah kasa kartace bazata aureniba Dagudu tashiga gidan labila tana tareda innah kawaiganinta sukai dagudu tafada daki tana kuka"" suka kalleta suduka sannan suka dubi juna innah tace dama nafadawa malam tayarda da maganar kine dan batasan kowaye kika zaba mata ba Ainidama nasan za ayihaka"" saikishiga kilallaso abarki"" labila kamar tayi kuka takama hanyar dakin innah tabita dakallo tace Allah yasa zatayarda tunda intakafe akan Abu bamaijuyata saidai nasan yanda kuke watakil tasaurareki Aisha✍🏼 ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠ Chapter 61 By Gentle Lady💃🏽 Taturah kofar tashiga da sallama khadija tana saman gado saidarzar kuka takeyi"" labila takarasa saman gadon tazauna Tadade tana kallonta daga bisani tadafata tareda kiran sunanta sahiba"" juyowa tayi tarungumeta tasake fashewa dawani kukan tace menene kikayi haka sahiba?? Dama dady ne kikecewa kinzabamun??? Meyasa zakiyi abunda kinsan bazaitaba yiyuwaba meyasa kikamun haka meyasa tasake fashewa dawani kukan Labila ahankali tasoma bubbuga bayanta tace sahiba saboda shine yachanchanci zama mijinki Duk da araina nayimasa kwadayin aurenki dabaisameni yace yanasonkiba wlh bazantaba cewa ya aurekiba please sahiba karkice bazaki aureshiba Dasauri tadago dagajikinta tana girgiza kai tace bazan iyah ba sahiba wlh tamkar mahaifina nake ganinsa bazan iyah auren babankiba""" Labila akufule tace kawai kifito fili kicemun bakyason babana kawai basaikincemun bazaki aure shiba Tanakai karshen maganar tamike daniyar fita dasauri khadija tasha gabanta tahade hannu waje daya alamar roko tace kigagarceni sahiba niba haka nake nufiba Amman kisamarmun wani wlh kowaye zan aureshi""" labila tacije lebenta nakasa tace shi mahaifin nawa baiyi makibane???? Hannunta khadija taja tace kizauna muyi magana" tafige hannunta komai zakifada kifadamun inajinki basai nazaunaba Tace haba sahiba Dan girman Allah kisaurareni"" tace ahakan kinamun kuka?? Dasauri tagoge hawayenta tace nadaina please kizauna Tanisa sannan takoma tazauna tajuya mata baya"" khadija tagirgiza kanta tace yanzu sahiba akan Dan wannan abun zakiyi fushidani??? labila tace awajenki yakedan nikam awajeba babban al a marine haba abudebaki ace ba ason ubana wlh kinbani mamaki danice wlh kowaye kikabani narantse saina aureshi tundahar kece kikafurta banice nace inasonshiba Khadija tace bazan iyaba sahiba haba dady dawanne ido zankalli mom??? Labila taja tsaki tace dayake kinsantane bakisantaba bakitaba ganintaba amatsayin matar mijinta zakishiga gidan tomenene Indai nizakiyiwa kara wlh banaso karkiji waidan tana mahaifiyata wlh nafison babana saudubu da itah farincikinsa shine nawa Kodawata yace yanaso zanyi ruwa inyi tsaki danganin yasameta ballantana kuma gudan sahibata"" tariko hannunta please sahiba babu musu atsakaninmu karki ki babana wlh yanasonki"" kirane yashigo wayar labila dama tundazu taketa ringing tasan dadyn tane tanadauka yace labila idan batayardaba kibarta""" nibari inwuce Tanisa tana kallonta tace kajiramu gamunan fitowa takashe kiran tanakallonta tace please sahiba"" Khadija ta sake share hawayenda suka saukomata tace bazan iyaba sahiba"" Labila tamike tunkafin khadija takarasa rufe bakinta"" tace magana takare tajuya dasauri tasake jawo hannunta labila tabuge dakata karkisake rikemun hannu tundakince bakyason babana" Wlh khadija kokiso kokarkiso nasan kinasonsa dasauri khadija takalleta tana girgiza kai tacigaba wlh kinasonsa tunranarda kikaganshi nasanda kinasonsa dan nakula dake sosai Yawan faduwar gabanda kikeji itace alamar harcikin jininki yakeyawo kuma ninasan bazaki iyah rayuwa bataredashiba kawaidai kinason hanawa kanki abunda kikeso"" tarufe bakinta tace bazakigane menake hangowaba Labila tadaga hannu tace ki amsamun zaki aureshi ah ko ah ah??? Tace kiyi hakuri please tayi maganar tanasake riko hannunta tajaye hannunta tawuce dasauri Khadija tabita dagudu tanafita tarufe kofar tayi hanyar gidan tana kuka hartana hadawa dagudu bawai komaitakeyiwa kukaba tanajin tausayin babantane"" Usman yanaganinta shima yafito yabi bayanta yana kiran sunanta"" kowaigensa batayibà saima tasake rugawa Khadija kofar gidan taduke tanata kuka kamar ranta zaifita gaskiya labila tafada idantace batasonshi tayi karya Amman abunda kunya mahaifin kawarta Inna ce tadafata"" tamike tafada jikinta tace inna yazanyi labila tayi fushidani" kinajifa abunda tayi"" innah tace nidai aganina ki amince kawai tunda kinasonshi Tace innah dangan takarmufa?? Tace Khadija meyasa kikeson haramtawa kanki abunda yake halal nee agareki"" ??? Kisani wani baya auren mijin wani hakazalika wani baya auren matar wani kidaina cutarda kanki nikaina nalurah dake tunranarda akayi walima kikashiga damuwa Saikiyi zugum kedaya kuma wani sa in sainaganki kina murmushi harnakanji kina magana da zuciyarki kinacewa tadaina babanki"" Adazaki iyah kauda kai Amman yanzu bawan Allah nan yataso tundaga kaduna yazo wajenki Kuma yasamu kawunki yamasa magana Kitunafa yarsa yayiwa magana batadauki komai arantaba tonamenene zakice baki yardaba Ta share hawaye tace toyazanyi inna kinagani tayi fushi""" innah tadafata tace dauko takalmanki kibita gidan kibata hakuri shima kibashi hakuri kice kin amince shikenan aiko Tagyada kai tanakara share hawayenta innah tace saikidaina wannan kukan karyace tilas taki akayi kuma tace to saida tasake gyara fuskarta tafita duk dahaka idanuwanta jajir suke kamar gauta"" ahankali take tafiya hartakai gidan gabanta kuma saidukan uku uku yakeyi Tanayin sallama cikin falon yana zaune saman kujerah yajingina kansa idanuwansa suna kallon silin da alamu tunani yakeyi kuma yayi nisa cikin tunanin Yanda hartayi sallama baijitaba kodan muryanta ta dusashe tagefen ido take satar kallonsa saitaga yakara kyau yanda yayi Sam fuskarsa ba walwala Dakin labila tashiga takosameshi abude harkuryar tawuce dan bata same ta falonba"" tana kwance saman gado tahau saman tajuyo dafuskarta wajenta Labila tasha toka "" khadija tace kiyi hakuri sahiba nibawai naki dad bane inaganin kamar cinfuskane na auri mahaifinki" "labila tace toshine me bashine yace yana sonkiba kuma ninayarda"" Tanisa shikenan sahiba indai hakan shine muradinki Na amince kiyi hakuri"""sannan kibawa dad hakuri naga kamar ranshi yabaci"" labila tace anki ahakura din 😏 tamurguda mata baki yanda tayi saiyabawa""khadija dariya tatintsire da dariya Labila takaimata dukan wasa tagoce tana dariya itama dariyar tasaka"" suka rungume juna"" suna dariya Khadija tace kije kibashi hakuri please"" labila tace kitashi mujedai inrakaki aibani nayilaifinba""😕 Tace kunya nakeji wlh""🙈 labila tace ke yanzu andaina jinkunya gaskiya dole nafara koyamaki darashi tayanda zaki yimasa kwarkwasa kiyimasa Farida ido Yanda idan yanatare dake bazaisake tuna kowaba"" khadija mayafinta taja tarufe fuskarta tanadariya Labila tace ashedai inada aiki agabana kunyar nan zanfara ciremaki tukun tamike mujeko Bayanta khadija talabe harsuka fita yana nan kamar yanda taganshi dazu Saidai yanzu murmushine kwance akan fuskarsa danyaji duk abunda sukefada"" bayajin muryan khadija saita labila Dan khadija kamar rada takeyi Kusa dashi taduka khadija talabe bayanta tasunne kanta haryanzu baidago ba kamarma baisan da zuwan suba labilace takirah sunansa daddy Batareda yadagoba ya amsa saikuma tayi shiru dantarasa mezatace masa"" saikuma tahau zungurar khadija Murya kasa kasa khadija tace dad kayi hakuriii cen kasar zuciyarsa yatsinkayi muryanta wacce tasaukarmasa da wata mugunyar kasala!!! Aisha✍🏼 ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠ Chapter 62 By Gentle Lady💃🏽 Yadago fuskarsa wacce take kumshe da murmushi idanuwansa yadorah akanta duk da tadukarda kanta"" yace laifin me akamun daza abani hakuri??? Aini yadace inbada hakuri gashi tasanadina nasa kinyi hasarar hawayenki masu tsada"" khadija kara sanne kanta tayi Labila ce tamintsileta"" itama tarama mikewa labila tayi tace inazuwa kafin khadija tayunkurah tuni labila taruga tashige daki tarufe kofa Dolece tazaunarda khadija Amman sai mutsuiniya take kamar wacce take akan kaya"" Usman haryanzu baidauke idonsa akantaba" Ahankali yakira sunanta khaaadeeeja hardawani Jan haruffan sunanta yanayin yanda yakirah sunanta yasaukar mata da kasala kasa amsawa tayi"" Saida yasake kiranta akaro nabiyu sannan ta amsa cen kasan makoshi""" yanisa inafatardai ba labilace ta tilas taki kibani hakuriba ..... Kai tagirgiza"" yace tomenene ra ayinki akaina nayimaki konayimaki tsufa ??? Bakinta tarufe tana dariya kasa kasa shima yadan saki dariya maidan sauti yace kifadamun gaskiya idan banyi makiba tayiyu nayi furfura dayawa bansaniba Wannan karon saida khadija tadago takalleshi ta sake sanne kanta kasa"" aranta tace anya kasan yanda kake kuwa??? Kamar matashi Dan shekara ashirin dabiyar"" Yace bakice komaiba??? Cikin jinkunya tace ah ah dad"" yamurmusa tokinyarda yanzu zaki aureni??? Tagyada kai Yace to Alhamdulillah insanarda malam kenan kin amince"" tace ah amman dady karatunafa""" yace hakane ainasan kunkusa gamawa koba ajinku daya da labila ba??? Tace ah ah ba skull dinmu dayaba"" suna riganmu zana jarabawa"yace shikenan badamuwa aikunkusa gamawa zan iyah jirah kikammala"" Shirune yabiyo baya kuma Usman yamaida kansa saman kujerah wani dadine yaketa ratsashi tako ina"" jiyakema tamkar gobene za adaurah masa aure da itah Farinciki yakeji marar misaltuwa Wanda baitabajin irinshiba"" shi run yayi yawa hakan yasaka khadija tasaci kallonsa saitaci sa a ba itah yake kalloba Takuramasa ido tana murmushi"" tanaganin yadan motsa tayi zumut ta mike dad nizantafi gida"" yace au harkingama firar??? Cikin zolaya yayi maganar batace komaiba Yace shikenan kigaida innah tace to dasauri tawuce hartanadan hadawa dagudu yabita da kallo cikin soda kauna saida tafita yasaukarda ajiyar xuciya mai nauyi yace Alhamdulillah Yalunshe idonsa yasake budewa yakwalawa labila kirah"" tana kwance tana game tace na am tareda mikewa tafito kusa dashi tazauna akasa tace waihar tatafi??? Yace ah tatafi"" murmushi labila tayi tace Allah yatabbatar da alkhairi yace Ameen"" sannan yagyara zamansa yace wanne irin sharadine kikace zakisanardani inhar tayarda zata aureni??? Labila tagyara zama tace inafatar ranka bazai sosuba??? Yace bakomai inajinki"" Tanisa kanta yanakasa tace banaso katambayi dalili akan komai dazanfada "" yace shikenan inajinki tanisa banaso kasanarda mom zakayi aure kabari sai ana sauran sati daya bukin Kamar yacemata menene dalilinta Saikuma yatuna tace karya tambaya shima anashi bangaren baidaniyar sanarda itah dansai kumuiniya yakeda maganar shiyasa yanzun ma dagawajen aiki yawuce kanon yace uhum inajinki saime kuma""tace inhar bikin yatashi karkabari mom tayi taron biki sannan koda tatambayeka zataje unguwa karkabarta Waifa awautar labila sai lubabatu tasamu fitane harzataje wajen bokanta abunda batasaniba lubabatu batazuwa ko ina bokanta madubinta danmuddiñ ba madubin tarasaba babu abunda zaikaita wajen bokan Yayishiru aransa yace kodai labila zargin mahaifiyarta takeyi??? Allah sarki batasan baburuwan lubabatuba harmatafini son inyi auren kawaidai halin matanne labila tacigaba Kawata bazata zauna bene Na biyuba kodai kabarmata naka kokuma mom takoma naka sahiba tazauna na mom din kaisaika zauna nabiyun Idan harkayimun wannan kagama mun komai saidai nayimaku fatan Allah yabaku zaman lafiya"" Yasaki murmushi taredacewa Ameen indai Dan wannan ne aibakomai"" maisaukine awajena"" yakalli agogon hannunsa yace wai ina abdulmajeed yashigane?? Tanadariya tace ainaturah shi gidan abokinsa tunda nasan zakazo yana iyah kwabsamana"" hajiya ma danasanarda itah zakazo shinefa itama tafita unguwa"" Yamike tokuwa bazan jirasuba aiki yanacen wlh nabaro muje nabaki sako sainawuce tace to tajuya daki tadauko mayafinta tafita"" yanagaba tanabiye dashi kofar gidansu khadija suka nufa labila takarasa tarufe kofar Tace dad koyanruwa bakashaba??? Yace taruwa nakeyi wacce nazo wajen ta tagudu tabarni dariya labila takamayi tace ayimana afuwa dad Motarsa yabude yadauko wani karamin kwali guda biyu yace gashi saikiduba kotayi biyu nasiyo saikidauki daya"" tace la dad nifa daya nafadamaka nitawa uncle baijima dasiyamun itaba waccema kasiyomana lokacin walima ya muktar yakarbeta ahannunta waibaiyarda tarika wayaba Yace toyanzu kikaimata aizanyi magana dashi yabarta da wayarta inaso zandinga kiranta munagaisawa tunda bakullum sai nakirah awayarkiba idankuma bakwatarefa Kije saiki saka mata chaji nibari nawuce tace tomungode Allah yakiyaye hanya yace Ameen yashiga motar yawuce tanadaga masa hannu Labila takunna wayar tadauki dayar tasaka number din dad tayi serving hubbyna daya number sa tasaka my everything"" Tayi murmushi taka she wayar tamiyar cikin kwalinta tawuce gidan tsakar gidan tasamu khadija suna labari da innah tanaganin labila tahau dariya Labila taharareta cikin wasa tace haka akefirah waidaga shigana daki kodanafito bangankiba tayi maganar tanazama tace wlh sainatashi tsaye naga alama sahiba batasan yanda ake tarairayar saurayiba Bacinma kiyita janshi dafirah harsaiyamanta inda zaije dareyamasa agarin nan"" inna banda dariya babu abunda takemasu itakuma duk labila tasata jinkunya"" Tamikawa innah tace gawayar sahiba dad yace abarta da wayarta zairika kirah suna gaisawa saurankuma idan yakirah kiki dauka dannalurah bakisan love ba"" Innah tace nadaiganoki labila kamfen kikewa dad"" tace bahaka bane innah sonake tutarmu tayi sama aikingane tayi maganar tanakashe ma khadija ido daya Takaimata duka tagoce tana dariya bari nawuce gida kitashi kisaka chaji kikunna bamamaki idan yakai office zaikirah yaji muryar maisanyinsa Idan yakirah kilankwashe murya kice helo my love tayi maganar tanayin Farida ido khadija tamike tabita dagudu tafita gidan tana dariya Inna ma dariya takeyi tace kecedai labila ce maishiga tsakaninku zaiji kunya"" kidauki wayar kisaka chajin tace to Wayar tadauka zuwa dakinta takunna wayar sannan tajonata chajii takurawa wayar ido fuskar Usman takegani ajikin glass din wayar sai murmushi takesaki *WACECE KHADEEJA!* Kubiyo yargidan Ibraheem domin kuji cikakken tarihin rayuwarta "" Aisha✍🏼 ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠ Chapter 63 By Gentle Lady💃🏽 Fateema shine sunan mahaifiyar khadija innar fateema Yar nigar ce "" sunanta hauwa"u mahaifin malam garba"" Dan kasuwane yanazuwa kasuwanni kasashe daban daban Matarsa daya"" sadiya dansu nafari Abubakar Amman amfikiranshi da garba"" saikuma tagwaye datahaifa duka mata hasana da Husaina daga garesu batasake haihuwaba Mahaifin malam garba acen wajen kasuwancinsa yabullah Niger yahadu da Hauwa" u kunsan bozayen Niger basucika bada yayansu ga hausawaba Acewarsu basada rikon Aure itah kuma Hauwa"u ta tsunduma wajen son buhari"". Babu yanda iyayenta basuyiba akan tafita harkansa tabuga kaidakasa tace batason kowa saishi Duka kuwa babu kalar Wanda batashaba Amman takekashe kasa tace shitakeso iyayenta sukace tosaidai tazaba koshi kosu awautarta saitace tazabi buhari Wannan shine babban kuskureñda tatabka Rashin bin maganar iyaye Sukuma sukace toduk abunda yabiyo bayan auren karta kuskurah tanemesu koda auren yakwabe saidai tanemi wasu iyayen basuba tace ta amince"" Yayan mahaifinta shine sarkin Niger baiso suyanke mata wannan hukuncinba Amman tunda tanace ita shitakeso saisuka cire hannunsu daga sha aninta sukace tacemasa yaturo Takuwa sanardashi ya turo iyayensa yabiya sadaki atake akadaurah masu aure sukace yadauki matarsa babu wani biki da akayi Taci kuka hartagode Allah gashi itace kawai awajen mahaifiyarta"" ranar sukataso daga Niger sukazo kano acikin danginta ko kuda babu Wanda yarakota Sadiya tariketa hannu bibbiyu duk da halayensu badayaba saboda Hauwa u tanada hakuri sosai itakuwa sadiya akwai fada dakuma mita Amman baruwanta daharkar kowa saifa idan antabata Amman Hauwa u koda dukanta kayi zata tambayeka Allah yasadai bakaji ciwoba😉 Shekaranta uku taredashi sannan tasamu ciki cikin yanabata wahala sosai haka tayita fama harta sauka tahaifi yarta mace sak kamanninta ranar suna yarinya taci sunan mahaifiyar buhari fateema suna kara anacemata yarbaba kamar yanda buhari yake kiranta tuni sunan fateema yabace sai yarbaba buhari yadauki son duniya yadorah mata Kamar babuwata ya agabanshi face itah yanda yakerawar kafa akanta kaikace baitaba haihuwaba hakan saiyasoma damun sadiya tanarayawa aranta bayason yayanta Watakilma magani Hauwa u taimata dantasan yan Niger matsafane yanda takejin labari saitasoma sauyawa Hauwa u idan yarbaba tamatso inda take saita tureta tanacewa matsanan dangin mayu aniyarku tabiku Kowani Abu Hauwa u tadafa bataci saitace ina nasani ko saida aka barbadeshi za aban Toni ba kwadayayya bace bataci kuma batabarin yaranta suci Saikuma takoma tanayiwa hauwau gorin danamiji tanacewa komaidai tsafin mutum dole yabarta kuma itace dagida bamai Yar maceba Tun abun nan bayadamun Hauwa"u haryakai yanadamunta gashidai batada wani Dan uwa dazata kaimasa kukanta yasharemata hawaye Mijinsu kuma bayazama kuma idan yana nan Sam sadiya batanuna komai agabansa sannu kan hankali tasoma ramewa tanafita hayyacinta"" tatsakure kullum sai buhari yasata gaba datambaya meke damunta tacemasa bakomai idan yamatsa saita fada masa saita azamasa kuka haryagaji yakyaleta bayan ta yaye fateema dawata hudu Kawai tahada kayanta tacewa buhari gida zataje shikuma yace bazataba tace saitaje yace totabashi yarsa yakarbe fateema tanata kuka tatafi tabarta sadiya tanagefe kokallonta batayiba Tundaga lokacin batasake waiwayarshiba shidinma bai waiwayetaba Fateema babu kalar ukubarda batashaba agun sadiya batajin tausayinta kokadan Tuntana karama hartagirma cikin wahala take"" lokacinda tagirma saitahadu dawani Muhammad shikuma dan yola ne bafulatani Suka Kama soyayya sunatsaka da soyayya ne sadiya tasoma rashin lafiya Hawan jinine yakamata gakuma mutuwar Rabin jiki damuwa tamata yawa hasana aurenta hudu abokiyar zama tahanata sakat duk inda tai aure sai abokiyar zama takoreta Itakuma Husaina tahadu dawata arniyar kishiya tamaida itah boyarta komai aikin gidan itah takeyinsa kuma miji baida halin shiga dakinda take hasalima dakin awakai take kwana Wannan damuwar ita tahaifarwa sadiya daciyo datagadai ciwon saigaba gaba yakeyi saita tara kowa fateema hassana Husaina garba dakuma buhari Tanemi sufaye mata"" laifinda taimasu"" kowayace batayimasa komaiba tana kuka takalli fateema tace Dan Allah yarbaba kiyafemun abunda naimaki son zuciya dakuma zugar makociyata itah takaini ga halaka nacutardake fateema narabaki da mahaifiyarki Ta sake fashewa dakuka buhari yace haba yazaki daurawa kanki laifi ai ba aimata komaiba tatafi danhaka idan kawai mailifi tonine"" tasake share hawayenta tace wlh bakada laifi malam nice naimaku asiri na farraku gabadaya wajen sukahada baki asiri!!😳 Tace kwarai kuwa lokacinda aka kawo hauwau wlh dazuciya daya nariketa tamkar Kanwata hartazo tahaifi yarbaba bantaba cutarda itaba Lokacinda naga malam yasoma fifita fateema akan Yayana sai nasoma jin haushi tawannan hanyarne shaidan yasamu yashiga zuciyata yadinga yimun huduba sainafara kyararta ina tsangamarta Danazauna inyita zaginta inacemata mayya" Amman bata taba fadawa kowaba saidai tabarwa zuciyarta watarana ina zaune saiga makociyar mu matar kabiru tashigo tasameni nayi tagumi tayita sallama banjiba alokacin Hauwa tana barci Saida tatabani sannan nazaburah nanisa hannuna taja zuwadaki tace menene yasameki kika buga tagumi kamar wacce tarasa mijinta Nadanyi tsaki nace dama shinarasa dasauki kinjikinji meyake damuna nalabarta mata komai shine tace nakwantarda hankalina akwai wani boka komai nakeso zaiyimun indai dakudi Duk danasan zuwa wajen boka baidakyau Amman shaidan yarufemun ido nace sonake kawai arabasu tabar gidan Shine nace Amman bazaniba saidai nabata kudin takarba tatafi waini wayone nayi saboda naji ance duk Wanda yatafi wajen boka kowani Dan tsibbo Allah bazai karbi ibadarsaba hartakwana arba in idankuma yamutu akan hanyarsa tagidan bokan yamutu kafiri waini nakizuwa domin natsirah Bayan kwana biyu takwawomun laya tace inkama bakin layar indaure dawani kyalle na kayan hauwau injefa amasai sannan tabani wani garin magani tace inbarbada kofar dakinta nakarba nayimata godiya Washe garikuwa tanabarci nalababa dakinta nayanko gefen zaninta nadaure layar naje najefata amasai nakuma barbada maganin kofar dakinta "" inatsakar gidan zaune nakwallomata kirah Yautaji nakirata rabonda nakirata hartamanta cikin fara a dazumudi tafito batasan ni damugun nufi nakirataba tana tsilga maganin sainaga tajuya daki tahau hada kayantaa!!! Aisha✍🏼 ☠ *HATSABIBIN BOKA!!!*☠ chapter 65 By Gentle Lady💃🏽 Amman saikuga adinga kyararta abunma yawuce gida har yan unguwa todakuma aikomai daga gida yake tashi sunga kunayi mezaihana suma suyi Rukayya tayita hakuri dasu hartakai sunazuwa sunacewa fateema in rukayya tabata Abu kartaci dantana bakincikin cikinda kejikinta Dayake fateema tanada hankali Sam bata daukar maganarsu Amman kunsan dawatace ahakan saikuga wata fitinar ta auku kaimiji kanacen kana nema masu abinci Bakasan ta inda fitina zatakunno kai agidankaba koda zaka farga wuta hartaci tacinye alokacin koda kaso ka sasantasu abun yafikarfin tunaninka Cikin fateema yacigaba dagirma haryanzu tanabaiwa rukayya girmanta" bata daukan zugar dangin miji sukuwa abunsu saigaba gaba yakeyi cikin fateema yanashiga wata Tara tasuntulo kyakkyawan danta kinkowa Wanda yarasa babansa sak Waiyo zokuga murna wajen rukayya musamman tahada walima saboda murnar saukar fateema lafiya kayanda tasiyawa yaron kuwa kowadanda mahaifinsa yasiyamasa basukai yawan nataba Ko maijego kala goma tadinka mata tayi gayyar abokananta sukansu kallonta kawai sukeyi da mamaki dangikuwa tunda sukaga fateema tahaifi namiji saikuma gori yadawo sabo Ranar suna akasawa yaro suna muktar harsu hassana saida sukaje biki"" taro yawatse su hassana dakin rukayya suka kwana sunsha firah washe garin suna suka koma Wata tsohuwace takekulada fateema hartayi arba in"" sukacigaba dazamansu lafiya"" saifa dangin miji idan sunzo gidan basakiran muktar dasunansa saidai sucemasa magajin gida!! Sam abun baidami rukayyaba harma abun yasoma bata dariya watarana tanazaune alokacin muktar watanshi goma dayake bayada kiuya hannuntama yake kwana nono kanshi baidameshi ba saidai idan yana kuka da anbashi ruwa shikenan Fateema tatafi wajen kitso da lalli tunsafe tabarmata shi sallama tajiyo anayi tata so tana am sawa tadage labulen kofa tace la la la Asma.u kece agidan nan??? Maraba maraba shigomana tadorah muktar akafadarta wacce akakirah dasunan asma u tawuce saman kujerah tazauna rukayya tace daga inakike haka cikin tsakiyar rana Asma"u taharareta tace zakice haka tundake bakyason zumunci aini karanima inazuwa tunda bakyason zumunci sainadauke kafata Rukayya tace habadai Yar uwa wlh aikine bayabarina fita ko kitso rabona danaje amun harnamanta saidai maman muktar takeyimun danzanen yawo Asma" u tamere baki"" rukayya tace rikamun shi nakawomaki ruwa tayi maganar tana mikamata shi tajaye jikinta dasauri tace wa ?? Ninadauki Dan kishiya Allah yasauwake Rukayya tayi dariya tace kice haryanzu halin yana nan???🤔 Tace hargobema indai akan kishiyane sai abunda yacigaba!!😕 . Rukayya tayi dariya tace Allah yashiryeki Kawata nidai bansan lokacinda zaki saki makamankiba kiyarda kishiya abokiyar zamace Asma"u tasheke da dariya tace inakika taba ganin anzubarda makamai afilin daga??? Shifa abokin gaba dakike gani duk wani kwantardakai dayakeyi na munafurcine soyake yashammaceki Dazaran yasamu sa arki kasheki zaiyi"" ance kakashe makashinka tunkafin yakasheka"" rukayya tace kedai kikasan wannan hadisin"" tawuce baridai inbaki ruwa yana akafadarta takawomata ruwa tasha Tazauna kusa da itah saiga muktar yasaki fitsari tace kai yaudai kasharuwa dayawa saifitsari kaketayi batagama rufe bakintaba yasaki zawo tuni yabata mata kaya Asma" u tayi saurin rufe hancinta wai itah doyi rukayya tana rungume dashi tanabuga bayansa ahankali haryagama taje tawanke masa tasauya wani zani tasakamasa wando Tadawo tazauna yihakurifa Kawata nabarki kedaya"" tajatsaki ahakadai zaki kare dabautar danwani rukayya tabata fuska tace menene haka Asma"u Dan mijin nawa shine danwani dakikecewa zankare abautarsa aidama bauta nazoyi Idan inason mijina yazama dole naso jininsa Asma"u tace tosannu daddawa dadi amre najinjina maki tobari kiji kokiso kokiki yaron nan dayagirma uwarsa yasani Dakike ikirarin bauta kikazo kefa yanzu hotoce kawai awajen mijinki" tayisaurin kallonta tace ahmana kehotoce saboda mijinki yanason Yaya sosai kingakuwa wacce zatayita haifamasa Yaya saitafiki fada keyanzu amatsayin Yar raino suka ajeki tanahaihuwa anabaki kinacinkashinsu dafitsari dazaran sungirma lokacinda dadi yazo maimakon kucidadin tare saitanunamaki kefa bakisan yanda dayake kwanciya amahaifaba Alokacin zata nunamaki itace tahaifi danta"" aini tunranar suna kikabani mamaki nasona kyaleki saikumà naga idan naihakan bankyautaba amatsayina na kawarki. Tagyara zama ninazomaki damafita idan kinaso??? Rukayya tayi shiru tace nidai mubar maganar nan nima indarabo zanga nawa Tayi saurin gwatseta tace yaushe??? Inda kinada rabon haihuwar aidakin haihu tunkafin yakaro aure gashi yayi Amarya daga zuwanta tasamu ciki zauna nan wlh saitacika gidan nan dayaya kekuwa kizama Yar kallo Shekararki takwas da aure tunyana talakansa futuk kika aureshi gashi yazama maikudi tamurmusa kibar ganin wannan daular wlh dazaran yamutu bazaki tsirah dakomaiba sai bakinciki Bazakiyarda da maganataba saiyafadi yamutu sukuma Yaya sukoma wajen uwarsu kinga bakiga yantusa yanzawo suntsere yanzu kikeda dama idankuma kikabari damarki tawucemaki tokece zakiyi kuka baniba nidai amatsayina na kawarki naga abunda zaicutar dakene nazo nafadamaki inkindauka ruwanki idanbaki daukaba ruwanki sainangaba zakiyi danasani alokacinda danasaninki bashida wata rana Ta mike nidai kinga tafiyata idan kin sake shawara kije gida kisameni ashirye nake da intaimaka maki sai anjima idan uwargidan Muhammad tadawo kimika gaisuwata tawuce abunta Kotadakai rukayya batayiba har fateema tadawo tasameta cikin wannan halin tatambayeta meyake damunta saidai tacemata kartadamu bakomai"" Kunsan shaidan shifa danwaje yakeso yasamu ya lababa yaitayi mana busa akunne hakanne yasamu rukayya maganganun Asma" u sukaita mata yawo azuciya taso takawarda tunanin takasa Sati daya dafaruwar hakan fateema tafara rashin lafiya anazuwa asibiti akace tanada ciki wata uku abunda yayi matukar tayarda hankalin rukayya sai aka yaye muktar akabarshi hannunta Kullum Muhammad yana nane da fateema mekikeso mene bakyaso rawar kafarda yakeyi yanzu saitasoma baiwa rukayya haushi hartasomajin haushin fateema Gashikuma cikin fateema yazoda laulayi komai taci saita amayar dashi "" sai Muhammad yatarkata aiki yadawo jinyarta watarana yana zaune yanabata abinci abaki saida tagama cinyewa tasoma kwara amai Saida ta amayardashi duka"" Muhammad duk yarude sai sannu yakemata rukayya tanazaune tana kallonsu yacemata taimakamun da Abu ingoge Kamar tace bazaniba saikuma ta mike tafita yacema fateema sannu kaitagyada yace yanzu mekikeso kici??? Kaitagirgiza yace haba uwar Yayana yazaki zauna dayunwa kisamu koda tea ne kisha . Kuka tafashe dashi tace banaso banajin dadin komai yakoma rarrashinta najito uwar Yayana Amman kinsan likita yace kirika cin abinci saboda Karin kafiyarki dakuma Dana dayake jikinki shiru tayi batace komaiba Rukayya kuwa sanda yakecewa uwar Yayana Kalmar tafada akunnenta tafara nanata sunan aranta lallai zancen Asma" u gaskiyane inhar fateema tacigaba da haihuwa agidan zatacika gidan da Yaya Idankuma hakan tafaru itakuma menene matsayinta wata zuciya tace Yar raino mana dasauri tace wlh karyane bazan yardaba Ganin tajima bata dawoba Muhammad yasake kwalamata kirah tazaburah tashigo dasauri tace yihakuri jinayi kamar kukan muktar nadauka yatashine sainaje naduba shiyasa nadade Yace bakomai yakarbi ruwan da abun gogewa yagogemata bakinta rukayya tanayimata sannu tanakuma harararta😣😂😂 Aisha✍🏼 ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠ Chapter 64 By Gentle Lady💃🏽 Tana fitowa kana shigowa. Tace maka gidansu zataje kaikuwa kacemata bazataba takafe akan saita tafi shine kace totabaka yarka Tabaka tatafi dama shine rabuwarku ance bazaku sake Neman junaba Nikuwa tundaga lokacin nayita ganawa fateema azaba naso tamutu harguba makociyata tabani tace nasakamata acikin abinci Amman dayake batada rabon hawala kwananta basu kareba saigashi akuyata uwar gargen da yayanta takunce daga daurinda naimata tafada madafa dayayanta sukacinye abincin alokacin tana wajen dibar ruwa Koda tadawo saidai naji tanasalati tana kiran sunana koda nafito damasifa sainaga abunda yafaru ga dabbobina wannan shine asalin abunda yafaro ciwona domin dasu nadogara akuya bakwai duka sukai musai Takaici yasakani nakilmawa fateema kashi nace itah tazubamasu guba dantana bakinciki da arzikina kaikuma saika yarda kasake dukanta taja majina kaji abunda yafaru tun alokacin naketa ganin i shara gashi Ya.yana sunyi aure abunda naiwa Hauwa suma anaimasu Ninasan abunda nashukane nakegirba wlh nayi nadama Dan Allah kiyafemun fateema yarbaba tana kuka tashare hawayenta tace bakomai innah ninayafe maki duniya da lahirah Buhari kam shiru yayi danyakasa magana saida tasake neman gafararsa yace nayafe naki sadiya bakece dalaifiba nine mailaifin tunfarko daban fifita son yarbaba akan sauran yayanaba dahakan batafaruba Hakika nikaina na aikata babban laifi duka yayanane kowanne amanace agareni baidace kafifita danka akan wani danba koda kafisonsa aranka kadinga yin kawaici musamman idanma yaran ba uwarsu dayaba hakan zai iyah janyo rabuwar kan iyalinka kekuma dakinkirani kinyimun nasiha aibawani abubane Amman kin aikata babban laifi wacce kika zalunta Hauwa inazakiganta kiroketa gafara kokinsan Allah baya yafe hakkin wani hakika hakkintane ke bibiyarki kamar yanda itama hakkin iyayenta yake binta Mun aikata son zuciya munbiyewa soyayya hakan yasaka batayi rabuwar dadi da iyayentaba sunce tazaba kosu koni tazabeni rashin bin maganar iyaye shine yajawo mata haka harkuma yashafi yarta Allah ya yafemana kura kuranmu suka amsa da amin tace malam taimako daya zakamun kaje Niger wajen danginta tayiyu takoma gidane idan kaganta kanemamun gafararta sannan kamaida matarka nasan haryanzu kanasonta ninasan ciwon nan nawa banatashi bane """ Yace nayimaki alkawari zantafi duk danasan abune mai wahala su saurareni dansuna ganin kamar nine silar rabasu dayarsu kidaina maganar mutuwa aicuta bamutuwa bace insha Allah zakisamu lafiya dakanki kinemi gafararta tace hmm kawai dan itah kawai tasan metakeji ranar jikin kowa yayi sanyi sukuku suka wuni washe gari kodasuka farka saidai sukaga gawarta tacika cikin dare tashin hankali sunganshi bakamar garba yanaganin mahaifiyarshi tashuka abunda bazai barta kwanciyar kabariba Sati biyu darasuwarta garba yamatsa aje Niger buhari yashirya suka dunguma hardasu hasana da Fateema"" Amman dasukaje gidansu Hauwa mahaifinta ko saurarenshi baiyiba yayimasa korar kare Dayaki tafiya fateema kuma tahau kuka bindiga yadauko yace kosubarmasa gida koya dirkesu da bindiga dole suka futa fateema tanata waigen kakarta wacce taketa kuka" dankuwa babu abunda yaraba Hauwa da fateema Agarin suka kwana buhari yayita tambaya koda tadawo garin akacemasa batadawoba tunda ta auri wani bahaushe tayafe gida aikowa yabargida gida yabarshi Washe gari sukadawo Nigeria saikuma buhari yakwanta jinta danyanzu soyayyar Hauwa tadawomasa sabuwa watanshi daya shima yace ga garinku Fateema takoma marainiya garba shike tallafe dagidan haryayi aure alokacinne Muhammad yafito daniyar auren fateema Muhammad yanada mata daya sunanta rukayya sunyi auren saurayi da budurwa amman haryanzu bata tabayin koda batan wataba Aurensu kuma wajen shekara takwas kuma shi yana masifar son Yaya Amman yanason matarsa hakan yasaka yakiya kara aure saigashi yakawowa wani abokinsa ziyara kano haryayi sati daya akasuwa yahaduda fateema an aiketa siyo kayan miya yabiyota haryaga gidansu kunji sanadin haduwarsu Garba dayaji yanada mata kuma gashi zatayi nisa dasu saiyace tahakurah dashi tasamu wani itakuma tace shiitake so tarihidai yasake maimaita Kansa domin fateema takafe kaida fata saishi Garba yanajin tausayinta dakuma halin kuncin rayuwa datashiga bayaso yatakurah mata sanin yanda soyayya take saiya amince Muhammad yaturo magabatansa akasarana suka biya sadaki suka kawo lefe akasa biki wata uku Wata uku sunacika aka dauramasu aure matar garba balkisu macece wacce baruwanta itace komai na fateema su hassana ma suntaka rawargani sun nuna bajintarsu amatsayinsu Na antys dinta garba yahada kudinda za asiyamata kayan daki acen yola akasiya akajerah mata babu laifi sunyimata kaya kamar diyar maikudi Ranarda za akaita har yola saida suka rakata sukaga gidan sun yaba sosai dahalin rakayya sai nan nan takedasu sunsan kanwarsu tayi dacen abokiyar zama Saida suka kwana washe gari kuwa dazasu taso sunsha kukan rabuwa haka suka rabu suna kewar juna saidai rukayya tayita basu hakuri Watan fateema uku saigaciki yabullu nawata uku danbata cilge wataba"" zokuga murna wajen rukayyya harma taso tafi Muhammad murna""batabarin fateema koda chokali taka war komai itah takemata hatta wankin kayanta Saikuma dangi sukafara jefan rukayya da habaici dama anacemata juya toyanzu zance yatabbata itace juyar gashi Amarya tasamu ciki itakuma batada aiki saidai taci takasayar Hasbinallahu wa ni imal wakil kalu innalillahi wa inna ilaihir rajiun waimenene amfanin yiwa wani gorin haihuwa??? Shinkeda kika haihu wani Abu kikayi yasaka kika haihu??? Wayonkine kokuma dabararkice??? Anasiyenta dakudi kokuma mulki zaibaki??? Itah dabata haihuba laifi tayiwa Allah ko anfada maki Allah bayasontane??? Waimeyasa mutane basuda tunani kisani duk wacce kikaiwa gorin haihuwa wlh hartamutu bazata manta dakeba kuma kema bakiwuce Allah yakarbe yayanda yabakiba sannan kidaina haihuwar aganina inhar wata acikin danginku matar yayanki ko matar babanki ko kanwarki kishiyarki inhar hakan yasameta saiki kwantarmata da hankali kice tacigaba dayin addua Allah maji rokon bawansane Aisha✍🏼 ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠ Chapter 66 By Gentle Lady💃🏽 Daga fateema har Muhammad basu lura dawani chanji tattare da itah ba saidaifa tadaina sakewa da fateema kamar da Saisuka danganta hakan da damuwarda tashiga narashin lafiyar fateema idan fateema talangaye wa Muhammad tana kuka sai rukayya taraya aranta duk kissace da kisisina babu abunda yake damunta Shedan yadinga yimata huduba tawanke kafarta tatafi gidansu Asma" koda tashiga da sallama tasamu mijin Asma u yanawankin kayanta yashanya wasu gakuma wasu tulin kayan sannan kuma gashi yana girki Yatara uban zufa sai sharcewa yakeyi rukayya tagaidashi sannan tawuce dakin rukayya saman kujerah tasameta tahakimtse tanacin naman kaji abun nan yamatukar bawa rukayya mamaki tana ganinta tatashi daga kishingidarda tayi tace yaukece agidan nan kodai batan hanya kikayi??? Rukayya Tanisa tace kusan haka"" ta sake kallon kofa tace anya Asma"u kinatsoron mutuwa??? Tace danayime??? Rukayya tace hmm abunda nagani mijinki kike sakawa wanki??? Tamere baki waisaboda dan ""wannan wayasa ya auroni idan bazai iyah daukar dawainiyataba Rukayya tace lallai haryanzu dasauranki karfa kimanta aljannarki tana karkashin kafarsa"" idan baidagaba bazaki shigaba Kunkumi tarike tace abudole tsufa da duwai aiyazama dole yadagamun inshiga""abunsaiya bawa rukayya dariya tace Allah yashiryaki Tace ameen bamaki addua ba"" 😕rukayya tace bawan nan banidai zuwanayi akan maganarmu taranar Asma "u tasheke da dariya tace bake bace idan kaga kigudu sagudune baizoba inazuwa tayi maganar tanamikewa Rukayya tabita dakallo yanda Asma u tagoge kamar wata hajiya miji duk yakanjame bakin kofa tatsaya tace isihu korufe bakinta batayiba saigashi dagudu yazo haryanacin tuntube yace mekikeda bukata rankiyadade Tayatsina fuska bakomai kafita waje kasha iska zuwa anjima karka dawofa saina kiraka"" yace shikenan godiya nake yajuya yafita dasauri Tasaki murmushi sannan takoma wajen rukayya wacce tasaki baki tanakallon abunda yafikarfin tunaninta Asma u tace Kawata inajinki " rukayya tanisa tace maganarda mukai ranar yanzu maganarda nakemaki cikine da itah Asma"u tace kadanma kikagani bake tsoron Allah ba"" rukayya tace yanzudai duk abar maganar menene mafitarda kika samamun??? Asma" u tagyara zama tace duk mafita tawuce irin tawa Rukayya tace kamarya banganeba Asma"u tace akwai wani boka sunansa *hatsabibin boka* aikinsa kuwa nantakene inhar kinyarda zakije wajensa tokeda kuka har abada Kunyi bankwana da bakinciki jinta ambaci sunan boka yasaka rukayya tazama tatsaye tace Asma u yanda nake ganinki ashema kinwuce nan boka dai! gaskiya danasan wannan itace mafitarda kikasamamun dabanzo gidankiba Allah yakareni da hatsabibancinsa Asma"u ta sake darawa tace aini gatanaimaki tundahar nakeson hadaki da babban boka Wanda babu kamarsaa aduk fadin duniyarnan Rukayya tace gatafa kikace ahakan??? Aibashima yadace akirah hatsabibiba faceke sunan yafi dacewa dake Asma"u tace kinga nidai bansakaki doleba ra ayine idankinji bazaki iyaba""kitafii haka kurum kefa kika kawo kanki banice" natilas takiba idan abun yadameki dakanki zaki dawo Rukayya tamike tace badai wajen *hatsabibin kuba* wlh bazaniba haka kurum ina zaman zamana kinzo kintayarmun da hankali duk tunani yadameni Tace kinga tafiyata Allah yashiryeku tawuce abunta Asma u tace tokigaida uwar yayan Muhammad wannan kalmar tana matukar tsayawa azuciyar rukayya Koda takoma gidan tasamu Muhammad gida sai lailayar fateema yakeyi taci abinci tanatayi masa kuka abun yasake kularda rukayya tanashiga da sallama tadage kanta tawuce fuuu kamar kubu buwa Fateema tace me akayiwa Anty kuma"" Muhammad yace tobadai mune mukabata mata raiba"" idan tahuce aizata fito dayake fateema batason magana saita kama bakinta Itakuma rukayya tayi tunanin zaibiyota taji tsit saita fashe da kuka tayi mai isarta dole ta share hawayenta ahakadai akayita gurgurawa da dadi ba dadi harcikin Fateema yakara girma tadaina laulayi ""cikin ta yana shiga wata Tara takama nakuda Cikin tashin hankali Muhammad yasakata amota zuwa hospital batawani jimaba ta sake haiho santalelen danta kinkowa Wanda yarasa kyakkyawa sak kamar muktar Zokuga murna awajen yan uwan Muhammad kamar suhadiye fateema""kayakuwa tashasu kamar hauka kokayanda Muhammad yatirka mata saiwanda yagani Sati yana zagayowa akayi suna wannan karon su hasana kawai sukazo Dan matar garba tana fama da laulayi Yaro yaci sunan Umar faruq"" anakiransa faruk yanbiki sukaci sukasha sukai kat kowa yawatse akabar maijego da yaronta Muktar kullum yana makale da fateema danyana mutuwar son yaron duk da ko anbashi baya iya daukarsa danyanzu shekaransa daya dawata takwas Fateema tanaganin yan sauye sauye atattare da rukayya Amman batakawo komai aranta tacigaba darainon danta" tuni rukayya tadaina sakewa muktar fuska Faruq yanada wata shida saigashi fateema tasoma laulayi tunda akace cikine da itah tahau kuka ita wlh bazata yardaba saidai azubarda cikin Shikuma Muhammad yace wlh baza a zubar dashiba shiyanason abunshi takaicima yasakaa tabaroshi asivitin Yanata kiran sunanta kowaigensa batayiba tanafita tatari Dan adaidaita tasanardashi inda zaikaita Muhammad raibace yabaro asivitin Anakaita gida tabiyashi kudinsa tafada gidan tana kuka"" rukayya tataso dasauri tace lafiyarki fateema ina abban faruq din??? Meyasameki kiketa kuka Batagama rufe bakintaba yana shigowa yace fateema Ashe haka kikeda taurin kai"" taballamasa harara tace dankawai kaibakasan wahalarda akeshaba da ajikinka yake aidabazakace hakanba"" Rukayya tace waimeyake faruwa niduk kuntayarmun dahankali tayi maganar tana kallon Muhammad Yace tambayeta gatanan"" tajuya wajen Fateema tace meyafaru cikin kuka tace wai Anty cikine dani Rukayya tace ciki nashiga uku harkin kuma samun wani cikin itah batasan inda maganar rukayya tadosaba tace ah wai Anty shinefa nace azubar waibaza a zubarba Haba kwata kwata shekarana nawa da aure ace inada yara har uku kumama ba wannan ba umar fa watanshi shida aikodan sabodashi zaiji tausayinsa Rukayya dai daka tahana wuri magana dangaba daya hankalinta yagama tashi lallai idan tayi sake maganar Asma u gaskiyace fateema zatacika gidan da yaya haihuwa kamar akuya😾 dama matane dadan sauki koyanzu watakil namijine zata sake haihowa Muhammad yakatsemata tunani wajen magana yace wlh fateema baza a zubarba ai wannan rashin godiyane kitunafa aurena shekara takwas Amman bansamu magajiba saiyanzu danake ganin gudan jinina kinaso azubar Yayana Na halak ne kuma inason kayana nibanki wlh kihaihu duk bayan wata taraba Rukayya Tananata Kalmar aranta *magaji* babbar magana dolene nadau mataki idankuma bahakaba inaji inagani gidan nan zai gagareni soyayya taci ubanta🙄 Koda tafarga har fateema tashige dakinta saidai taji Muhammad yana bubbuga kofar yana hadata da Allah tabude itakuma sairusar kuka takeyi Dasauri yafita idonshi jawur kaman Wanda akadaka yaja motarsa yayanki titi tsaye nahango rukayya kamar mutum mutumi tarasa inda zata saka kanta Tana nan tsaye tajiyo sallamarsa bayansa kuma"" gwaggo rabiee ce kanwar mamarsa tashigo dasauri rukayya tana gaida itah kokallonta batayiba tayi hanyar dakin fateema tasoma bubbugar kofar bude Fateema nice haba Yar kwarai irin albarka kibude kinji fateema Fateema CE tabude takoma tazauna tacigaba da kukanta"" gwaggo rabie takarasa saman kujerar tazauna Muhammad shikuma yanatsaye yakuramata ido Gwaggo tace haba mai babban suna yazakiyi haka kitausayawa babangida mana dayake haka suke kiransa sunan babansune Tace ai wanann abun farincikine abun alfarinkine ace kinada ciki menene amfanin azauna saidai aciyarda mutum yana tula kashi Indai faruq ne karkisamu damuwa babu abunda zaisameshi dazaran anyi wata uku zanzo inkarbeshi saina yayeshi kekuma saikiyi rainon danku Kinji fateema kiyi hakuri tunda kinga babangida yanason yaran nan"" kinji mai babban suna"" fateema tashare hawayenta tace tahakurah wani dadine yalullube Muhammad Bayan tagama bata baki sannan tafita suka gaisa da rukayya tace kiyi hakurifa wlh hankalinane atashe shiyasa bangankiba"" Tace bakomai ai nikam nasan taciki naciki dankuwa ranar rukayya kasa barci tayi saidai takai gwauro takai mari Mafita dayace dolene inkoma wajen Asma" u muje wajen bokan dankuwa banada wata mafita wacce tawuce wannan ai Allah maiyawan gafarane idan nadawo saina nemi ya yafemun Shikenan ai Allah yaga zuciyata wannan abun zaicutardani kuma Allah yace tashi in taimakeka Dan nanemarwa kaina mafita bazai kamani da laifiba Dawan nan shawarar hankalinta yakwanta takoma takwanta tanamai murmushin jindadi "" wai hauka shaidan yazo yalailayomata wadansu banzayen maganganu wai Allah yace tashi in taimakeka aibata wannan hanyar yace abiba Koyace acutarda wani dansamun farincikin wani waifa tace idan tadawo tanemi gafarar Allah kwarai Allah gafurur raheem ne Amman Allah baya yafe hakin wani shinbatayi tunanin tanakan hanyar kobayan tadawo tahadu da ajalinta kafin tatuba ??shin idan taje gaban Allah tanada hujjar dazata kare kanta ??indai abunda tafada shine hujjarta lallai hujjar banzace dankuwa batariki hujjaba Rukayya abunda batasaniba duk Wanda yaje wajen boka to Allah zai zaremasa imaninsa tamkar yanda akezare lakka ajikin kashi Aganinku duk wacce taje wajen boka tanada sauran imani kije kawai dankisa acutarda Yar uwarki ke kodama badaniyar cuta kikajeba baikamata kijeba Dawan nan bakin kudirin takwana washe gari lomar fari tunda take bata taba fitah gidanba batareda izinin Muhammad ba saigashi tayi satar hanya Koda taje gidan tasamu Asma u zaune mijin yanayi mata tausa akafafunta tanaganinta tasheke da dariya tace bakebace Tamaida kallonta wajensa tace sai abamu wuriko kanata kallonmu wiki wiki da she gun idanuwanka tuni yasanne kansa kasa Yamike yafita tamaida kallonta wajen rukayya cikin fara a tace zauna Kawata tazauna tana kallonta"" tace koyauma zuwa kikai kicimun mutunci dani da *hatsabibin boka???* Rukayya tashare hawaye tace bar maganar wasa Kawata zuwanayi kitaimakamun yanzufa waikuma tasake kunsar wani cikin Tasake fashewa da kuka"" tace wlh komenene zanyi indai zatabarmun gidana banason buda ido naganta cikin gidan dashegun yayanta Asma "u tasheke da dariya"" tace bakebace dai ainafada maki"" rukayya tace toyazamuyi Asma u tagyara zama tashinfida mata dukkan dokokin shiga dajinda *hatsabibin boka* yake dakuma saradansa idan zata iyah Tace komenene wlh zan iyah Asma" u nidai banaso naganta agidan To Rabie da Aisha saiku shirya Dan tare zakuje kudibo mana labarai😂😂 karnaji kunce bazakubà dankodà igiyane sainajaku inda Wanda zàshi kàllo yamun magana naga kamar motar takusa cika🚌 Aisha✍🏼 ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠ Chapter 67 By Gentle Lady💃🏽 Tace indai wannan ne karkisamu damuwa indai akwai shegun to komai kikeso zakisamu aidama tsiyar abu rashin kudi gashi kanagani Abu yafikarfin ka Amman idan akwai kudi hmmm komai kikeso zaki iyah tambayarsa kidairike sharadansa nazuwa wajensa sannan kuma duk abunda kikagani adajin tsapappene kar wani karambani yajaki kitaba Tam Rukayya tace nikam mezantaba Kawata ??? Tayi maganar tanarike habar gemunta tace nifa ko acikin kaset naga boka jikina har ciccira yakeyi saboda tsoro ballantana kuma inga wannan da idona"" tabdi kedai kawai muje Asma "u tace waikina nufin yanxun??? Hmmm kinsan kowacce kasa yake kuwa??? Rukayya tace shinbama kasar nan yakeba??? Asma "u tace babbar magana aiyafi karfin zama anan kenan cikin arha zakisamu komai tobari kiji taraba yake Rukayya tawaro ido tace tarabadai tarabadai wacce nakeji anafada??? Asma" u tace kawaimakuwa itah"" rukayya tabuga tagumi tace Toni tayama zanje taraba nidabantaba zuwaba??? Asma"u tace nima kaini akayi gashikema zankaiki bake daya zakiba dazakice kinbace hanya" rukayya tace bazaki ganebane"" taya zansanarda Muhammad zantafi taraba??? Wlh bazai narniba"" Asma" u tace Amman ke bahwanyace inbanda haka tayazaki sanarda miji ainahin inda zakije barikiji dazaran kinkaida kudin kamar anasaura kwana uku kicemasa Na gaiyaceki biki garinmu Kanwata za ayi aure wacce take hannun yayar mamana kaduna take Kinga kwana biyu zakicemasa dazaran munje muyi abunda yakaimu mudawo koyakika ganie Rukayya tace kinkawo shawara maikyau Amman Anya zaibarni naje waniguri inyi kwana biyu??? Asma"u tace barikai aiyanzu yanda yakeson fateema wlh koda wata daya zakiyi bakidawo ba bazaiwani damu sosaiba Rukayya tayi shiru sannan tace kinga inayin wani dashi kuma jibi za ayi kwasa tawace inaganin kawai saimu tafi tace shikenan dazaran kudin sunshigo hannunki saiki kirani kiyimun magana"" tace shikenan sukai sallama tawuce gida Allah yasa Muhammad baidawoba da sadade takoma dakinta danko sallama batayiba ko Fateema batasan dafitar tata Illaikuwa tana karbar kwasarta tasanarda Muhammad zataje garinsu kawarta Asma u kanwarta za ayiwa aure yace shikenan kwana nawa zakuyi tace biyu nakeji yace shikenan yadauki dubu hamsin yabata yace tayiwa Amarya sayayya tayi murna sosai dama tana tunanin kudinta kamar bazasu isah ba"" Washe gari tashirya dama tasanarda Asma "u Fateema tayimata Allah yakiyaye tace Ameen"" aranta kuwa tace hmmm bakisan wannan tafiyar ta kibace ta musamman Tanafita tayi gidan Asma "u tasameta hartashirya itakawai takejirah tanazuwa suka wuce dayake tasha suka shiga motar bawai jirgi bane basu suka kai taraba ba saikusan goshin magrib Rukayya tace itakam tagaji susamu gurin kwana"" Asma u tace nifa duk nazo garin nan gidan wata magajiya nake kama hayar daki kinsan hotel akwai tsada idankuma kinada kudi isassu saimuje Rukayya tace sujedai gidan magajiyar suhuta kafin magrib hakan kuwa akayi sukaje cen dama tunda bajimawa sukeyiba dakin magajiyar takebasu Dan ita ma tana dai dagacikin costomomin *hatsabibin boka* duk wacce tsautsayi ya Kaita fadawa hannunta hardai idan taga kinaja anasamun kudi akarkashinki haka zatakai sunanki wajensa atsafeki akafeki gidan tayanda bazakisake dagawa wurinba harsai idan kinmutu Duk wacce akaiwa auren dole tagudu kokuwa tsautsayi ya afka kanta tayi ciki kafin aure idan tagudu daga GIdan uwayenta tashiga duniya Tahaduda tambai yarduniya tokuwa tazama nama"" akwai wani kwalli datake bawa yaranta suna shafawa Wanda takarbo wajen *hatsabibin boka* muddin suka shafashi dasunyi ido hudu dakai tosaidai wani kariyar Allah idankuma harkasoma harka dasu bazakataba bariba Danduk kakwanta dayaranta bazatasake jindadin mu amala dakowacce maceba"" takenta kuwa yaranta bawai saida dare sukefita kasuwancinsu ba .sunazuwa kasuwanni dakuma manyan kantuna inda sukasan manyan attajirai sunazuwa hakazalika sunazuwa bikin manyan yankasuwa Dakuma gamnoni kodakuwa ba agaiyacesuba saisunje Kuma ba ahanasu shiga kodakuwa basuda ticket din shiga Suna zaune sunazuba firarsu rukayya tamike danjin ansoma kirah asma"u tace inakuma zakije?? Takalleta da mamaki tace banganeba sallah zanyi bake kikace da anyi sallah zamu wuceba Asmau da magajiya suka bushe da dariya magajiya takalli asmau tace wannan dai sabuwar zuwaceko??? Asmau tace ah wlh bakigantaba sai ahankali Takalli asmau tace inasharudan da nafadamaki kafinma muzonan??? Ita rukayya sam tamanta Tace kash wlh namanta Kawata"" Asma u tace akwai aikikuwa wlh idan kikai kuskure baburuwana dake dashine dannafada maki duka dokokinsa kikace kinji kinganie Rukayya ta marairaice fuska tace yazakice haka aikinsan daban mantaba bazance namantaba waye baya mantuwa aduniya Asmau tace kowa yanayi Amman inaso Kituna da abudaya wlh *hatsabibin boka* baya yafiya duk kikai masa laifi babu imani zaihukuntaki danhaka kikama kanki mufita lafiya kodai ince kekifita danni qalau zanfita Rukayya tace tonima ai idankuma harwani abu zaisameni ai anyi ba ayiba kenan ina amfanin badi barai"" kedai kawai kisake sanardani zankiyaye asmau takalli magajiya wacce taketa busar dariya itama tadarasuka tafa sannan tasake korawa rukayya bayani Ana kare sallah suka kama hanyar kauyenda yake bakin hanyarda zata sadasu da dajinda yake aka saukardasu suka kama hanya harsuka iso fadarsa dajin dai yana nan kamardai yanda su lubcy sukazo saidai akwai wasu sauye sauye Danyanzu duhuwa tayiwa wajen yawa kaikobakin dajin ka iso dole katsorata gabadaya yanzu yatsafe dajin kogonda yakecikima yanzu koda kazoma baka ganinsa tayama zaka iyah shiga dajinda yake dauke damiyagun namun jeji da abubuwan firgitarwa Kafin kakaima tsakiyar dajin kagama yawo saidai uwarka tahaifi wani""" haduranda sukecikin jejen bazasu faduba saidaikayi kokarin hana kanka zuwa gurin Abudayane zaitserar dakai idan yasan dama wajensa zakazo kodahakan ma saidai katsaya bakin jejin karufe idonkaa saikakirah sunansa takezakaji anyi sama dakai karka kuskurah kuma kabude idonka idankuma kabude Namun jejin dakuma miyagun gungun aljanu masucin naman bil adama sune zasuyi kalaci danamanka yaga yaga za aimaka tayanda kowane guntun naman jikinka bazaiwuce tsoka dayaba"" Dakaji iska talafa bakamar sanda aka surekuba saikabude idonka take zakaganka kabayyana agaban *hatsabibin boka* idankuma zakubar dajinma hakane anan zakurufe idonku saikuji ansake sunkutarku koda zakubude ido kuganku bakin dajin daganan saikuwuce abunku Asmau tasanarda rukayya yanda zasuyi kuma tace karta kuskurah tabude idonta rufe idonsu keda wuya sukaji ansunkuceku anyi sama Sauran kadan rukayya ta kwamtsa ihu"suna bacewa bakagansu ko inaba saicikin babbar fadar *hatsabibin boka* Naga sauyi sosai awajen gakuma kayan alatunan tako ina saikuma tarin kayan tsafinsa rukayya tanayin ido hudu dashi jikinta yasoma rawa Asma u itace tasoma koramasa jawabi kafin yace tayi shiru yasan komaiketafe dasu Yamaida dubansa wajen rukayya yace mekikeso ayimata??? Tace sonakeyi asaka fitina datashin hankali atsakaninsu banaso tabargidan farat daya yan uwansa zasu iyah zargina Itakuma inaso kowa yatsaneta harta mutanen unguwarmu saita gammace mutuwarta akan rayuwarta yayanda take takama dasu suma surika gudunta Daka karshe idantagama wulakanta saiyasaketà alokacin duka yan unguwa dama ta ishesu sai kafitarda duka soyayarta azuciyar mijina Bayan tagama korah jawabi *hatsabibin boka* yakece dawata mugunyar dariya tamkar jakiii nakuka yace wannan babu abunda yafishi sauki awajenmu Shanruwa ma zaifishi wahala"" yace menene amaryarki tafiso ayanzu??? Rukayya tayi shiru alamun tana nazari 🤔sannan tace agwaluma da gwaiba Yagirgiza kai yace bashiba"" tayi shiru dagabisani tace mangwaro gaudee yace todashi za ayimata maganin Rukayya tace to Amman inaza asamu mangaro ayanzu tunda balokacinsa bane *hatsabibin boka* yace wannan aikin mune banakuba dazaran kunkai gida zakisamu mangwaron ajakarki saikibata tasha Zamusamu mujiya dakuma makauniyar jaba da itah za ahada ayimata maganie yandakikasàn mujiya hakazata koma cikin al ummah ke mujiyamà saitafita gata dankuwa zatarika fitarda wàñi wari Wanda makotankuma saisungaji da doyin sannan zamubaki wata laya kijefa amasai Dazaran kinyi wannan aikinki yagama Aisha✍🏼 ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠ Chapter 68 By Gentle Lady💃🏽 Maganin wannan layar kuwa dazaran kishiyarki tabuda baki daniyar yin magana wa mijinki wani mugun doyi zaiji kamar ya surnana hancinsa acikin shadda"" rukayya batasan sanda tayi dariyaba cikin jindadi tace tomenene ladar aikinka ??? Batareda ya kalletaba yace yar uwarki tasani saita sanardake tajuya daniyar yiwa Asma u tambaya yadaka mata tsawa wacce tahargitsamata kwanya yace ba anan zakiyi maganaba kibari saikun bar nan kubacemun daganie Atsawace yayi maganar asmau tace saikirufe idonki rukayya dajikinta yaketa faman rawa tayi saurin rufe idonta saikuma akasuresu saibakin dajin Ai rukayya. Tanabude idonta taganta bakin dajin tayanka dagudu daniyar komawa cikin dajin dantafirgita tuncikin fadar bokan saida Asma u tayi saurin riketa tajata dasauri sukabar wajen zuwa bakin hanya Dakyar sukasamu motarda tamiyardasu gidan magajiya rukayya saida taganta gidan tasoma saukarda numfashi ko abinci batatsaya ciba takwanta barcin wahala yasureta su magajiya sai dariya suke Dan asmau tafadamata yanda sukayi da rukayya Washe gari kasuwar garin sukaje tasiye dabbobin ta aikamasu dasu tacewa rukayya kinga yanda zakiyi duk lokacinda kikasake dawowa rukayya ta kwalalo ido tace wa???😳 Badainiba aiduk Wanda kikagani lafirah kaishi akayi wlh nishegen tsorone dani ni inama tsammanin sanda yadakamun tsawar nan anyama basuma nayiba?? 🤔 Gaskiya inhar aikin nan yayi aini shikenan banida wani buri aduniya indai tabarmun gidan to mezai miyardani"" ?? Asmau tace akwai kuwa Kawata kinmanta akan kishiyarki kawai akayi aiki to idankuma yasake auro wata anan gabafa??? Rukayya tanisa tace kumafa hakane Amman anya zan iyah zuwanidaya wlh natsorata sosai bantaba shiga tashin hankali irin wannan ba"' Asma"u tace nafarkone aibazaki sake jinhakanba Tace shikenan garin suka sake kwana washe gari sukadawo gida "" saida tahuta gidan asmau sannan tawuce gida da sallamarta Tashiga gidan tasamu fateema zaune tanashan iska da itah da muktar Dan gwaggo takarbi faruq .. Tana ganinta tasaki fara a la Anty sannu dazuwa wlh yanzun nan nakezancenki araina inatunanin kokin taso"" kujerah taja tazauna tanacire hijab tace wlh kuwa tunsafe mukataho yazaman gidan Fateema tace babuwani dadi gashi abban faruq anturashi wajen wani aiki jiya Amman inajin gobe zaidawo duk zaman gidan ya isheni gashi ban tambaya ba dasainashiga makota Rukayya tace Karma kisoma bakigani nikaina baburuwana dashiga makota yanzufa duniyar nan mutum akekiyo ba dabba ba Fateema tace aibama zanfitaba"" rukayya tasaka hannu cikin Jakarta saikuwa ga mangwaro guda biyu tafitar tanacewa ga abunda kikafiso nasiyomaki ai fateema tanayin ido hudu damangwaro yawunta suka tsinke"" abunkada maiciki tanakarba batawankeba babu maganar bisimillah kawai takama gabtar mangwaro Wani shu umin murmushi rukayya tasaki aranta tace taki takare fateema "" nantake tashanye dayan tadauko dayan tafasa sai muktar yaceshima sai tasammasa takilla tabashi kamar rukayya tahana saikuma takyale dankar fateema tadauka akwai wani abun Ta sake gabtar mangwaro tana lunshe ido saboda dadi tace wai Anty ina kikasamu mangwaro alhalin yanzun balokacinsa bane??? Rukayya tadauko bokiti tace baridai inkara maki dankarki fadi tana dariya tace bafa santi nakeyiba kumama koda santin nayi aibalaifi kinkuwaji yanda mangwaron nan yakeda zaki??? Rukayya tace inazansani aikinsan nibanashan mangworo"" fateema tace hakane naman ta wlh hartashanye mangwaron bata ahamoba tacewa rukayya dakinsani deyawa kika siyomun Tace ayya wlh nima akan hanya naganshi sauranshikawai danasan kina sonsa sosai nacewa driver yatsaya dakyarma nasamu yatsaya"" Fateema tace Allah sarki nagode Anty"" rukayya mikewa tayi tace baridai indan mike kafata kafin la asar barci nakeji wlh fateema tace tosaikin tashi tawuce dakinta tana murmushi Washe gari tundasafe tajefa layar acikin masansu tazuba ruwa yabiruwa yafada cikin shaddar dadare koda Muhammad yadawo fateema tayi barci baiko kalli kofar dakintaba yashige bangarensa Rukayya tana ganinsa tahau tsallen murna washegari dasafe tanadaki saiga fateema tashigo tana yakunar fuska tasamu guri tazauna tagaida itah ta amsa dasakin fuska Saikuma tayi shiru rukayya tace yadai maman faruq??? Kamar tayi kuka tace Anty ashejiya abban faruq yadawo Amman baitasheniba Rukayya tace ah watakil yalurah kinajin Da din barcinne"" tanisa Anty aibahakan yasababa sai idan yanzune zaisauya"" Rukayya tace toki kirashi mana"" nimadai jiyan banganshiba saidasafe danaga kaya afalo nasan yadawo Fateema tace wlh nakirashi yafisau ashirin yaki dagawa bansan laifinda naimasaba"" rukayya tace kisake gwadawa dai haka fateema tayita gwadawa hartagaji takoma dakinta Yinin ranar takasa cin komai harwashe gari kwanadaya rak hartasoma ramewa"" tana tsaka datunani kawai saiga Muhammad yafado dakin dasauri takalleshi kamar zatayi kuka Yanayinda taganshi yamatukar furgitata kafin tamike yahau dukanta batasan hawaba batasan saukaba tuntana yunkurawa daniyar tatashi tagudu hartakasa tayi kwance shikuma gabadaya bayagani yasa kafa yahalbeta aruwan cikinta wata mugunyar karar wahala tasaki take jini yasoma fita takafafunta Muhammad baikyaletaba saida yaga bata numfashi sannan yayarda bulalar yafitaa fuuuuu Saida yafita rukayya tasadado taga aika aikarda yayi damakuwa tanaganin zuwansa tashige dakinta ganin tanamasa magana yawuceta fuuuu dariya tasheke da itah tace inakuma soyayyar take ayanzu??? Muktar yana gefe yana kuka yanakirah amma rukayya tadaka masa tsawa tace munafuki rufewa mutane baki" muktar yasake bare bakinsa yacigaba dawani kukan saida tasake katsamasa tsawa wacce tafirgitashi shima atake yaja zuciya numfashinsa yai sama Ta sake bushewa da dariya sannan tafita tadibo ruwa ta yayyafamusu kusan taresuka far fado muktar yashige jikin fateema yana kuka Fateema bayan tagama nazarin abunda yafaru da itah Wanda take gani tamkar mafarki"" tasake fashewa da kuka"" mai tsuma zuciya Takalli rukayya tace Anty me yake shirin faruwa danine haka?? menaiwa Muhammad yayimun wannan dukan kamardai Wanda bashida imani?? Rukayya tace waikina nufin shine yadakeki?? Toyanibanji shigowarsaba fateema tace wlh shine Anty Rukayya tace kekuwa laifin mekikai masa??? Tace wanne irin laifi Anty wlh banyimasa komaiba"" rukayya tace to Allah ya kyauta tawuce abunta fateema tabita da kallon mamaki kamar bataga halinda take cikiba "" Rukayya tanafita takirah asmau tanadauka tace yee Kawata aikifa yanakyau"" asmau tace banafada makiba Tace ainagani yau Muhammad yalakadawa Yar iska shegen duka inajifa kamar tayima bari"" asmau tace toyanzu tana ina??? Rukayya tamere baki tace tanadakinta kwance inda yabarta Asma u tace yazakiyi haka aizatayi saurin zarginki banafadamaki dakissa akehadawaba yanzu kidauketa kuje asibiti dagacen kicema ayimata wankin Mara idan akwai sauran Matsiyacin yayo waje"" Rukayya tace toshikenan dasauri takoma dakin tasamu fateema tasake suma" fita tayi dasauri tasamu Dan tax dataimakon wata makociyarsu aka kai fateema asivibiti Likita yatambayi menene yayi sanadin zubewar cikin??? Rukayya tace aifaduwa tayi Amman ayimata wankin Mara karyazama ciwo ajikinta"" alokacin har anjona mata Karin ruwa Suna nan harkusan la asar lokacin fateema tafarfado Amman bata bude idontaba"" tanata tunanin wannan lamarin""" kwananta uku asiviti Muhammad bailekoba gashi likitoci sunbar zuwa gurinda take kaibartasuma har wadanda sukejinya daki daya duk sun sauya daki Aladole tasallami kanta tafito duk Dan adaidaitan da tatara baya tsayawa gashi jikinta baiyi kwariba tana tafiya tana tsayawa tana hutawa hartakai gida Gashi tafiyace mainisa ajigace takarasa gidan tashige dakinta tafadi kwance tafasheda kuka muktar ne taji yadafata tadago takalleshi duk yayi damau damau cikin kashi tasake fashewa da kuka maitsuma zuciya saida tayi mai isarta tahakurah dankanta Dakyar tatashi tashiga kichin dinta tasulala taliya sukaci bayan tawankemasa jikinsa haryanzu bataji duriyar rukayyabà Ashe tana makota tabar muktar shikadai cikin gidan Wasa wasa fateema abusai gabayake batajin sanyi wajenkowa saiwajen rukayya danyanzu saitakwashe watadaya batasaka Muhammad a idontaba Duk ranarda abun yacizoshi zaizo yayimata shegen duka gabada ya yan uwansama sundauke kafarsu daga gidan Gashi tanada zurfin ciki ballantana takirah tasanarda su Anty hasana halinda takeciki saidai ciwo yayita cinta ahankali"" Kwanaki sunata tafiya sati haka watanni haka shekaru haka fateema ta lalace tayi bakiii kirin wacce takefara"" alokacin muktar shekaransa shida aduniya yayi wayo sosai hakazalika shine kawai kedan kwantarwà fateema dahankali Watarana dadare tanakwance zafii yadameta tatashi tawatsa ruwa tadauro alwala"tanashirin kwanciya saiga Muhammad yafado kamar dagasama Tatsorata daganinsa dantasan babu abunda zaikawoshi dakinta idandai badukanta zaiyiba Aisha✍🏼 ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠ Chapter 70 By Gentle Lady💃🏽 Yanisa yana kallonta yace kikwantarda hankalinki yata nine nan zankwatomaki yancinki"" tayi saurin kallonsa tace taya baba aikuma aikingama aiyagama"" Yace ninasan yanda zanyi zanmiyar mata da abunda taimaki"" inhar kin amince dahakan"??? Taja majina tana kallonsa tace idan har nayarda amiyar mata da abunda tamun menene banbancina da itah??? Tanisa ninabarta da Wanda yayi rana dakuma faduwarta koda nayarda amayarmata tunda babu aure tsakanina da Muhammad aikin banzane nikawai nabarta da mahaliccinta indai duniyace aigata ga duniyar niyauma zanwuce garinmu danba kinciki zai iyah kasheni anan idan inatunoshi Malamin yayi murmushi yace hakane yata dama nayi tunanin hakan Amman tundakince kinbarta da Allah bariga Allah yafi" yagyara zama Amman kitsaya kikwana biyu akwai taimakonda zanbaki kafin kitafi"" Tashare hawaye tace kayi hakuri baba niyau gida zantafi"" banason sake kwana garidaya dashi malamin yace dolefa kiyi hakuri dantafiya bata samekiba. Kinkuwasan abunda ketare dake barta mijinki ko yan uwanki idan kikaje babuwanda zaikalleki dankuwa abunda yake ajikinki kokinfita babu mai motarda zaidauke ki kinkosan bazakije gida akafaba Fateema tayi shiru kamar mai tunanin wani Abu saikuma tace shikenan zata zauna"" tundaga ranar malamin yasomayimata rubutu tanasha dawani garin maganie"" dayayiwa hadi da habbatus sauda da turaren miski dawadansu kalolin turare yahada dazuma farar saka akadama daruwan zanzan kullum dasafe saisunsha chokali daya Da itah da mukhar harnatsawon sati daya"" bayan sati daya saigashi tasoma wani irin a mai baki kirin da gudajin mangwaro aciki hakashima muktar ammanshi bayawa sosai danshi baici dayawaba yanayin cizawa daya yaji tsami saiya Yar Abunda tagani yanzu shine yasake tabbatarmata da gaskiyar lamarin"" saida tasake kwana biyu malamin yayimata kudin motar saida zata tafi tarambayesu sunansu Matar tace sunanta khadija mijinta kuma ibraheem ta sake yimasu godiya harwajen shiga mota yasa aka Kaita tundasuka shiga motar tashiga duniyar tunani harsuka kawo kano Tahau Dan adaidaita zuwa unguwarsu koda tashigo duk yawanci suna masallaci wajen sallar magrib dasallama tashiga gidan tasamu matar Yaya garba tana kada miya Ta amsa sallamarta tataso taga kowacece tanaganinta tace yarbaba !! Kece da magribar nan lafiyadai??? Saikawai fateema tafashe dakuka tafada jikinta Tace yau nabani nidiyar mutum biyu jikar mutun hudu menene kuma yafaru yarbaba"" ??? Fateema batace komaiba taci gaba dakukanta anahaka garba yashigo dasallama yayi tsaye yana kallonsu yace kukan wanakeji kamar yarbaba??? Bilkisu tace wlh itace malam niduk ta tayarmun dahankali "" jinta ambaci sunan yarbaba garba yazoda sauri shima yahau tambayarta jikinsa harrawa yakeyi danyana tsoron ace abunda mahaifiyarsa tayiwa mahaifiyar fateema shine aka sake maimaitawa Fateema yanda taga hankalinsu yatashi saijikinta yayi sanyi anan take sanardasu aurenta yamutu sukai tambayar duniya tafadamusu meyafaru haryasaketa tace laifi tayimasa takisanar dasu komai harsuka gaji sukasamata ido Dakin ta tashare takoma ciki washe gari su hasana sukazo suma babuyanda basuyiba Amman bandakuka datakemasu idan sun matsamata da tambaya dole suka kyaleta garba yaso yaje yola din Fateema tace karyaje tunda saki uku yamata menene amfanin zuwan tunda koyahakurah bakomawa zatayiba Aranta tace aikoda akwai sauran igiyar aurena dashi bazan komaba ballantana komai yakwabe yace shikenan Ahakan tacigaba darainon cikinta haryafito batafirah dakowa inba muktar ba"" gashi ciwo yanacinta gayawan tunani"" cikinta yana shiga wata tara tasanarda matar garba in Allah yasauketa lafiya intahaifi mace khadija takeso asamata idankuma namijine ibraheem Bilkisu tace banda abunki kibari saikinsauka mana saikifadawa yayanku"" murmushi tayi Wanda rabonta dayin irinsa andade tace inaso komenene nahaifa asakashi islamiyya inaso yayi karatun sosai kullum maganarta kenan Ranar wata juma" a cikin dare tatashi da nakuda muktar ne yasheka yana bugawa su balkisu kofa dama bawani barci mainauyi takeyiba dasauri ta mike tafito waje Dakin tashiga dasauri tarufo kofa fateema tayi matukar galabaita tafita hayyacinta saikusan asuba tahaihu Kojuyowa batayi taga abunda tahaifaba raiyayi halinsa bilkisu taduka tadauki Yar tayankemata cibi tawanketa tagyara wajen garba yanakofa tsaye da muktar yana kuka Saifita take tana dawowa tadaicemasu ansauka ansamu mace Amman batasanardasu. Yarbaba tarasuba saida tagyara wajen tashirya jaririyar takuramato ido yarinya tamkar uwarta babu abunda yarabasu Hawayen tausayinta ne suka sauko akan fuskarta Allah Sarki kekuma taki jarabawar kenan fita tayi tabasu yarinyar takoma takimtsa fateema Fuskarta tayi haske fayau tamkar tana murmushi kamar kayi magana ta amsa rayuwa kenan "" rayuwa bawani abubace dazaran anzaremaka rayuwa takomai takare Duk kwanbonka komai kudinka saifa kadandani mutuwa menene abun dagawar ??? Dazaran anzaremaka rai yanda kasan mutum mutumi haka zaka koma shikenan taka kuma takare babu sauran jindadi masu bururruka aduniya Allah yasa mucika da imani Ameen Tadade dakin sannan tafito garba yace yamai gejon tana lafiyadai ko ??? Tagyada masa kai kawai alokacin hawayenda take boyewa suka karasa sauko wa takauce idonta danta goge Amman haryagani dasauri yashiga dakin tana kwance inda tahaihu ahankali yataka zuwa inda take yaduka yashafo fuskarta yace Allah Akbar Allah yasa kinyi kyakkyawar tafiya yatofa mata addua sannan yamike alokacin ansoma Kiran asuba Yakarbi yarinyar yayimata huduba da sunanda mahaifiyarta tace yamikawa bilkisu yakalli muktar yace muje kayi alwala muwuce masallaci bamusu yawuce yayi alwala shima yayi sukatafi masallaci Bayan an idar yasanarda liman akayi sanarwa za ayi za na izarta da karfe goma muktar baisan meyake faruwaba saida yaga mutane sunsoma cika gidan sannan hankalinsa yatashi yatambayi garba meyake faruwa ne Bawani boye boye yasanarda shi yayi tsammanin zaiyi kuka saiyaji kawai yace Allah yajikanta yamatukar bashi mamaki gashidai karamin yaro taredashi akai mata sallah har aka Kaita makwancinta Tundaga ranar rainon khadija yadawo hannun muktar dayake matar garba yaranta biyu duk mazane batasake haihuwaba daga garesu madara akarika bawa khadija Allah yarayata tuntana karama she gen wayo ne da itah makaran tarsu daya da muktar kowakuma yadakarmasa Kanwa kowaye saiya rama mata bayaso yaga kukanta kokadan Shikeyimata wanka da kwalliya akanta yakoyi kalaba danbaya kaita wajen kitso tunda yakaita sodaya yace masu kitson mugayene kwarai suke kitsawa danmugunta "" shikuma ahankali yakemata anayi anashan minti kuma bata kuka Tana primary 2 yagama makarantar yashiga babbar makaranta soyayya maikarfice atsakaninsu shine uwarta shine ubanta ko yayan inna balki suka daketa bayajin kunyar kowa zairama mata Sannu kan hankali tanazuwa boko tanazuwa islamiyya Amman tafi bada karfi islamiyya datadawo boko tawuce islamiyya sai magrib ake tashinsu idankuma ranarda ba bokone karfe bakwai nasafe sukezuwa sai magrib Tun tana yarshekara biyar takai hizif hudu kuma dazaran anyimata karatu nantake take daukesa akanta lokutta dai sunata tafiya khadija tanasake girma"" tanagama primary shikuma yanashiga ss 3 " tashiga itakuma jss 1 alokacin tanada shekara goma shabiyu"" yana gama secondary skull yashiga bayero university"" alokacin khadija takusan sauka alokacinne suka hadu da labila tadawo kano dazama saita shiga islamiyyar su waje daya suke zama Allah yahada soyayyar su waje daya saigashi kuma ashema makotane soyayarsu tayi nisa sosai kullum zakagansu tare alokacin muktar bagida yake kwanaba cen makaranta yake kwana idankuma bakaratu yakanshiga gari yayi aikin karfi yayiwa khadijar sa siyayya "" tuni tabashi labarin sahibarta dasuka hadu duk yakirah waya maganarta kenan sahibar ta"" su gwaggo hasana da Husaina duk sun hayayyafà kowace yaranta biyar duk sungirma Amman muktar shine babba sai yayan uncle garba sulaiman da dahiru suma suna bayero Tana ss1 muktar yatafi kasar waje waje karatu dansosai yanaso yayi ilimi yazama maikudi bayason kanwarsa tayi kuka anan gaba Amman ranarda zaitafiii tasha kuka dakyar tabarshi yatafi Tundayaje baidawoba saida yakwashe shekara biyu anyimasu walimar sauka dukda khadija tadade dasauka ba ayi walimarba akace sai ansamu kamar mutum dari duk dahaka sai aka kaita ajin hadda alokacin yazo yaga khadijarsa tasake girma kyanta yasake fitowa kamanninsu da mahaifiyarta yasake bayyana tana ss 2 lokacin suna shirin shiga ss 3 bangaren karatun islamiyya kuma hartakusa hardace alkur ani Muktar baramin dadi yajiba yanda kanwarsa tazama hafiza suna zaune tana rubuta wani hadisi acikin littafinta muktar yakurah mata ido yanata faman murmushi Ajikinta taji kamar ana kallonta tadago saisukai ido hudu itama murmushin tasakar masa tace Yayana meyafaru??? Murmushin yasakeyi yace idan ina kallonki nakan tunoda mahaifiyarmu Kamanninku daya saidai kawai kindarata haske kadan dakuma wushiryar da kikeda itah bayan wannan bakuda banbanci hatta Dan abun nan naki dimpull tanadashi akowanne saitin kumatunta Yanisa please Kanwata karkisa soyyya acikin rayuwarki kamar yanda nadade inasanardake mom tace tanaso kiyi karatun islamiyayya sosai yanisa banason kibiyewa abokai dannasan yanzu a skull kananun yarama zakagansu suna soyayya Hawayene suka sauko akan fuskar khadija take muktar yarude yataso daga kan kujerar yaduka gabanta habarta yadago yace kuka farincikina Maganatane tabata maki rai ¿kaita girgiza tace bahaka bane Yayana natunoda mom ne inama nima nayi rayuwa da itah inji diminta kamaryanda kowa yakejin dimin mahaifiyarsa Kuka tafashe dashi maikarfi muktar baisan sanda shima yafashe dakukanba labila shigowarta Kenan tanufo dakin tajisu suna kuka duk dabaya yabata hakanne baisa taga fuskarsaba saida sukai mai isarsu sannan muktar yayi karfin halin soma lallashinta ganin zaimike labila tayi saurin juyawa tafita batareda sungantaba Kwanansa biyu yakoma baisake dawowaba sai lokacinda khadija akaimasu walimar haddace al Qur ani Dalilinda yasaka labila tacewa Usman sunan mahaifiyarta akasamata dan kawai taji yangidan suna cemata sapna wannan sunan kuma muktar ne yalakaba matashi yanajin dadin sunan idan khadija tace saboda mene bayakiran sunanta saiyace ai sunan umma ne to itama hakan tasanarda labila shine tarike A Takaicedai wannan shine ainahin tarihin rayuwarta dakuma tushenta babukuma Wanda yasan wuyarda maman khadija tasha sai muktar danbaimanta komaiba shiyasa yakeganin anyama zaiyarda yabawa wani khadija??? *KYAWON TAFIYA DAWOWA* Aisha✍🏼 ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠ Chapter 69 By Gentle Lady💃🏽 Tasoma jadabaya"" tanabashi hakuri hannunsa yadorah akan labbansa yace shitt alamar tayimasa shiru takekuwa tarufe bakinta hantar cikinta tana kaduwa Kusa da itah yakarasa yajaye zaninda yake jikinta yajata akan gado yasoma wasada itah tamkar bayacikin hayyacinsa"" Sam yaubayajin haushi dakuma warinta kodan yana cikin matsananciyar bukatane oho Fateema Sam tamanta awace duniyar suke duk abunda Muhammad yayi mata tamantashi awan nan daren ashedai darabon khadija atsakaninsu domin rabon khadija ne yatasheshi abarci haka kurum yaji yana bukatar kwanciya damace Wajen rukayya yasoma zuwa saiyasamu tana al ada dayake wani baya haihuwar danwani harzai koma daki yaji bazai iyaba kawai yatunkari dakin fateema saigashi baiji komaiba harsaida yagama biyan bukatarsa Aizunbur yamike kamar Wanda yayi mantuwa kawai yakalleta itama shitake kallo tana murmushi tsaki yaja yawuce abunshi abun ma saiyabata tsoro anya dadyn faruq kansa daya kuwa mikewa tayi ta tsarkake kanta tadawo takwanta Tundaga ranar batasake sakashi acikin idontaba har aka kwashe wata uku talurah lallai cikine da itah"" gashi batajin dadi saiyawan ciwon ciki yaudai takudurah aranta zata sameshi tànemi izinin zuwa asiviti danciwon cikin yana matsanta mata"" Tana dakon jiranshi harbarci yadan figeta cen tafarka dasauri tasuri hijab dinta tasaka tafita zuwa dakinsa taturah da sallama saikuwa tasamu dakin bude tayi hamdala takutsa kai tareda sallama Suna zaune dashi da rukayya sunacin naman kaji rukayya saizuba masa shagwaba takeyi shikuma kamar zaimaida itah ciki saboda soyayya"" Bakisake fateema take kallonsu Dan sallamarda tayima abakinta tamakale ganin yanda suke soyewa. Amman kullum rukayya cemata takeyi itakanta muhammad yadaina kwana da itah yadaina sake mata fuska "" wasu hawaye masu zafine suka sauko akan fuskarta Muryar Muhammad taji yadaka mata tsawa kewacce irin jakace zaki shigomun daki cikin irin wannan yanayin kuma kiyimun tsaye akai Fateema tagoge hawayenta taduka kanta nakasa tace kayi hakuri nakatsemaku jindadinku wlh banda lafiyane kwana biyu shine nakeso intambayeka gobe zanje inga likita Yace bazakiba tashi kibacemun daganie"" takalleshi cikin mamaki tace Muhammad bafa wasa nake yiba katausayamun mana damezanji dawulakancin da kakemun koda ciwonda ke jikina??? Afusace yamike yace watoma ninakemaki wulakanci??? Lallai yarinyar nan kinsamu damar rainani dankawai inasake maki fuska tokarshen walakanci kije gidanku nasakeki saki biyu kimaza maza kifitarmun gida kafin nakirga goma Kwatakwata neman hawayenta tayi tarasa saitayi murmushin takaici tace nagode Muhammad balaifinka bane Nice dalaifi da nanace saina aureka Babuyanda Yayana baiyiba Amman nace saikai Amman kasani babu inda zanje sainayi idda Kafinma tarufe bakinta yace agidan ubanwa zakiyi iddar Tamike ahasale tace agidan uban Yayana kuma babu inda zanje sainayi idda"" yace wlh bazakiyi idda agidanaba ke kijema na iyarda sauran sakin sai inga inda zakiyi iddar tunda ba uwarkice tabani gidan ba Fateema tace wlh karkasake zagarmun uwa yace idankuma nasakefa "" tace sai inrama ai uwarka bafin uwata tayiba kafin tarufe baki yadaga hannu zaimareta Tarike hannun tace Karka sake wlh barganin kadakeni ada nakyaleka dajarar soyayyace dakuma aurenka dayake kaina yanzu Kuma babu kodaya danhaka bazanji takaicin ramawaba Ta sake masa hannu tacije lebonta nakasa zanbarmaka gidanka Amman kasani bazantaba yafemakaba bantaba cutar kowaba nikuma duk Wanda yacutardani bazan yafeshiba wannan alkawarine tanakaiwa nan tawuce abunta Sam kuka yabacewa idonta Zatafita yace dawo dawo ko kallonsa batayiba yafada dakinta yadauko muktar yana barcinsa yajawoshi kamar Wanda yadauko kayan wankii Tana kiciniyar bude kofa yace wazakibarwà wannan shegen dannaki tajuyo afusace tace shegen ubansa aibadashi nazoba danhaka babu inda zanidashi inkaga dama kabarshi yamutu tafita dasauri tabanko kofa Tanafita yajefo muktar waje yarufe kofar gidansa kukanda yakwantsane yasakata waigowa dagudu tadawo tarun gumeshi tahau rarrashinsa gabadaya unguwar tayi tsit kukan karnuka kawai kakeji yanatashi Tashi tayi tagoye muktar abayanta dukda babu zanie tasoma tafita gabadaya tsoro yafita ranta tayi tafiya mainisa hartabar unguwarsu sosai haryanzu kowa batahadu dashiba "" muktar haryakoma barciii gashi tagaji dole tasamu wani wuri tarabe tacire dankwalin kwanta tashinfida takwantardà muktar tazauna saiyanzu tasamu damar yinkuka Tasoma kuka maidan sautiii tsayin min tuna kamar ashirin taga anyadomata fitila maihaske hannu tasaka takare fuskarta tacigaba da kukanta Ahankali mai fitilar yatako kusa da inda take yakashe fitilar yadan rage tsawo yana dubanta yace baiwar Allah mutum ko aljan??? Batareda takalleshiba tace inaruwanka karabudani"" kaje kayi abunda yake gabanka"" yanisa naji Amman amatsayinki Na mace mai rauni baidace inganki anan ba kuma inkyaleki nimafa inada Yaya kamarki bazanso nima Yayana susamu Kansu a irin wannan yanayinba inaso suma ataimakesu Tace gawanda kebukatar taimako ko??? Toni bana bukatar taimakonka"" kabarni Dan Allah tasake fashewa da kuka"" Mutumen ya murmusa yace shikenan tunda bakyaso Amman bazan bar yaron nan wajen nan ba kinga gidana cen dasafe saikishiga maidakina tabakishi yayi maganar kawai yadauki muktar Tabishi da kallo komotsi batayiba bayan tafiyar sada jimawa saigashi taredawa ta mata alamu sun nuna matarsace yace kinganta nan yayinuni da Fateema Matar takaraso wajenta tace haba baiwar Allah kitaso mana kinkosan karfenawa yanzu??? Itakanta matar muryanta ta maibarcice dagaji mijinne yatasheta babu musu kuwa tamike tabi matar hargidan dakinda suka kwantarda muktar nan suka nunamata sukaimata saida safe Itakuwa babu maganar barci a idonta harsafe bayan tayi sallah tana lazumie saiga matar tashigo dakayan kari tagaida itah sannan ta ajemata tace kisamu kici malam zaiyi magana dake tace to Duk datasan bazata iyah cin komaiba"" tatashi muktar yayi alwala yayi sallah sannan tabashi abun kari yaci bayan haske yagama mamaye gari rana takunno kai saiga matar tasake dawowa wajenta tace kitaso yana kirah bamusu tamike tabi bayan matar"" Harwani daki tasameshi zaune saman buzunsa gatarin littafai nan agabansa dakuma allo da Qur ani tasamu gefe tazauna kanta yanakasa tagaidashi Ya amsa cikin sakin fuska duk kunya takama fateema data tuno yanda sukaidashi jiyan yakatsemata shirunta yace yarinya hakika nalurah kamar kinacikin damuwa Tunjiya la akarida yanda naganki dayaro acikin dare kuma cikin wannan muguwar shiyar'" inaso kisanardani abunda yafito dake daga gida Shiru tayi nayan dakiku sannan tasanar dashi""komai yace wa iyazubillah Allah yakaremu dasharrin shaidan yata wannan mugun asirine akaimaki domin arabaki da mijinki Gaban fateema yabada rasss dasauriii tadago kanta idanuwanta sunakawo kwalla tace asiri kuma baba??? Tomena tarewa wani dahar yakeso yashiga tsakanina da farincikina???? Yace yata abubuwa dayawa alabarinki kincemun matarsa bata taba haihuwaba??? Fateema tagyada kai yanisa kekuma gashi kinyi harbiyu ba mamaki itace dawan nan aikin Fateema tayi shiru tana nazari ta tuna jiya dadare datasamesu dakinsa duk abunda akeyi rukayya kotado kanta batayiba saicin nama takeyi abuntaa fateema tashare hawaye tace bashakka idankuma hakane Anty tacutarda rayuwata tafashe dakuka Saida matar malamin tasoma rarrashinta tanabata bakii Aisha✍🏼 ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠ Chapter 72 By Gentle Lady💃🏽 Tundaga muktar har khadija babu Wanda yaruntsa harsafe khadija takwana kuka kafin safe wani zazzafan zazzabine yakamata jikinta yagashe kamar wuta Sallar asuba kanta dakyar tayi gashi jiya bataci abinciba"" dasafe inna takawo mata abun karinta tatasheta tace takoshi Babuyanda inna batayiba Amman takici dataga zatadameta tace zataci inna tanafita tasake gyara kwanciya"" tana nan kwance har azahar muktar baishigo dakinba Inna tasake kawo abincin rana tasamu nasafen bataciba"" ta ajemata tafita dakin muktar tayi saita sameshi zaifito kenan yana ganinta yadansaki ransa yagaida itah Ta amsa tace idan zaka iyah rarrashin sarkin zuciyar cen kaje wlh yaukoruwa batasha ba rabonta da abinci tunjiya dasafe babu yanda banyi da itah dasafe ba tanuna masa kaga karinta nasafe yanzu danakai narana nadaukoshi Yayi shiru sannan yace shikenan yajuya zuwa dakinta koda yaturah kofa idonta rufe yake yataka harbakin gadon yazauna yakuramata ido Yasan tasan shine dangashinan idanuwanta sunsoma zubarda kwalla duk da arufe suke" sunanta yakirah bata amsaba"" baidamuba yace kitashi kici abinci Nandinma banza taimasa yaturah hannunsa daniyar yatasarda itah mugun zafinda yaji shiyasa yacire hannunsa dasauri batareda yayi niyaba Cikin tashin hankali yace khadija bakida lafiya Daman??? Meyasa baki sanardaniba duk arude yake maganar dasauri yafita yacewa innah kishirya ta yanzu zandawo da doctor yadubata yafita dasauri yana dauko waya cikin aljihunsa Abokinsa Abubakar yakirah yasanardashi yana kano yanzu haka yanason ganinsa "" yace toyasameshi gida danyanzu Hutu yake yace toganinan tafe Yanagama wayar yatari Dan adaidaita zuwa gidan sa bayan yakirasa yace yakaraso saiyafito motarsa sukashiga zuwa gidan Yashiga yasanarda innah zaishigoda doctor tace to saida yashiga yasamu khadija kwance yagirgiza kansa sannan yafita""" Yashigoda Abubakar din yagaida innah sanan sukashiga dakin "" yataba jikinta dazafi sosai sannan ya aunata"" haryagama abunda yakeyi muktar yana kallonsa Yatashi tsaye yana kallon muktar yace me akaimata halan??? Muktar yace mefa akaimata doctor mekedamunta??? Yanisa yawan tunanine yahaifar mata da damuwa gakuma kirjinta yanazafii Tunyaushe rabonta da abinci?? Jiki asanyaye yace jiya" yace mujeto asiyomata magani dole aimata allurar barci domin tasamu barci ko damuwar zataragu Yace tomuje yayi maganar yana kallon khadijar taresukaje dashi akasiyo maganin da allurar yabiya sukaje inda masu fura damun injin yasiyamata suka wuce gida Dakyar yasamu tasha furar sanann akaimata allurah takwanta yanunamasa yanda zatasha maganin idan tafarka yayimasa godiya yarakashi bakin motarsa sundade suna firah sannan yatafi hankalin muktar duk yana wajen khadija Kodayakoma yasamu tayi barci kusa da itah yazauna yabuga tagumie yana kallonta"" wasu hawayene suka saukomasa yasadan yatsansa yataresu Yana nan har akayi la asar yatafi masallaci yadawo yazauna ba itah tafarkaba saigoshin magrib yataimaka mata tawatsa ruwa tayi sallah taci abinci tasha maganie takoma takwanta Sallamar labila sukajiyo tsakar gidan tagaida innah sannan tafada dakin tanakiran sahib bata rufe bakiba sukai ido hudu da muktar yasake tsuke fuskar nan Itama saita dauke kanta tace inawuni bai amsaba itama batadamuba saman gadon tahau tace meyasameki sahiba??? Khadija saman kafarta tahau saitafashe dakuka nantake labila tafara kukan tace me akaimaki sahiba??? dan Allah kiyi shiru Muktar yanazaune yanakallon ikon Allah"" innace taji kukan yayi yawa tashigo tozakufara sana ar takuba kuyiwa Allah kuyishiru Kojinta basuyiba itama tsaye tayi tasaki baki kamardai yanda muktar yayi tsayin mintuna goma khadija tayi shiru saikuma takoma rarrashin labila sahiba kiyi shiru kinji kar zazzabi yakamaki Saida tagama rarrashinta sannan tace inayan tafiya??? Da murmushi tayi maganar labila tace tunjiya naso inkawomaki da dare harzanfito sainaji raina abace nakoma daki nayita kuka jiya wlh banruntsaba zazzabi yarufeni Yanzun Karin ruwama akaciremun tanunawa khadija hannunta tace inatashi nacewa hajiya kinzo tacemun ah ah shine nataso ingako lafiya Khadija tasaki wani kayatacceñ murmushi tana kallon labila tace sahiba lafiyata qalau Nima rashin ganinkine yahaifarmuñ da damuwa Amman yanzu tunda naganki Alhamdulillah Tace nima wlh sainaji nawarke taresuka sakarwa juna murmushii"" muktar yamike jin ansoma kiran sallah yafita baicedasu komaiba Aransa yana tunanin wannan wace irin soyayya ce sukewa junansu aidole khadija tace tanason baban labila Kuma batai laifiba Amman anya nizan iyah barinta ta aureshi??? Nifa tsoron matan yanzu nakeyi dawan nan tunanin yatafi masallaci Inna ma fita tayi domin tayi sallah suma sukayo alwala sukai sallah anan suka zauna sunata labari yawancin firarsu duk akan karatunsune na islamiyya har innah tagama abincin dare sukaci gabadayansu sunware tamkar basuyi ciwoba"" Muktar yadawo yasamesu suna tafirah yadade bakin kofar yana saurarensu basu ganshiba dan hankalinsu baya nan juyawa yayi yabar kofar dakin Saikusan karfe Tara labila tayi gida saida sahiba tarakata sannan tadawo tanashigowa gidan tasha toka zuwa dakinta batajima dazamaba Saiga muktar saman gadon yazauna yana kallonta yace sapna kenan wannan fushin duk ni akeyiwa ko??? Gashi kinware tunda kinga kawarki Amman tana tafiya kinkoma kina fushi Dadago da sirarun hawayenta tace Yayana ciwona azuciyata yake bawai afuskaba nayi kokarin boye damuwa tane saboda labila muddin tasan inacikin damuwa zata matsane saina sanarda itah menene damuwata dakuma silar damuwar Idanhar nasanarda itah Kaine kake fushidani wlh bazata sake kallonka da mutunciba"" ninasan labila batunyauba danhaka nake boye damuwata duk lokacinda muke tare Yanisa yanzu khadija ninake fushidake??? Kodai kece kike fushidani"" hawayenda suke kan fuskarta suka karasa saukowa yace please nifa bakuka nace kiyimunba "" tace Yayana taya zanyi mushidakai Kaine ubana kuma Kaine uwata Kasharemun hawayenda uwayena ne yakamata su shafemun banida wani babban farinciki aduniya Wanda yawuce inga nafaranta maka rai Yayi murmushi khadija kenan aiyanzu banada wannan kimar tunda har nahanaki soyayya Amman kikayi dama bayada mata dadan sauki Amman khadija mai matafa kuma harya manyanta Gyara zama tayi tana fuskantarsa tace Yayana duk da bansan dalilinka nafurta hakanba nasan kasan wannan baharamun bane Shimai mata baza a aureshiba tosabodame??? Koshidin bamutum bane??? Kasani mata sun linka maza sosai idankowanne namiji mata daya zai aurah sauran matan kumafa wazai auresu??? Yayana idan kai aure nan gaba kana bukatar kari kaima saiwacce kakeso tace batasonka tunda kaima kanada mata"" shinzaka saki uwar yayankane saboda kanason Karin aure??? Idan kasaketa ka auri waccen kasake ra ayin karawani aurenfa??? Aganina mai mata bashida wata illarda za ace aurensa bazai yiyuba sai idan ansan shidin ba nagartaccen mutum bane tanisa banyimaka wannan maganarba waidan kabarni Na auri dadyn labila Tundahar bakasonsa wlh nahakurah dashi zansanarda labila kayimun wani mijin kokuma inbika cen kagama bangantaba ballantana inji damuwa Amman Yayana nasan kanada dalilin fadin haka Dan Allah kasanardani meye dalilinka Aisha✍🏼 ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠ chapter 71 By Gentle Lady💃🏽 Wayar taketa kallo tana murmushi"" saiga kirah yasoma shigowa cikin kira ar sudes tuni khadija talunshe idonta saboda jindadin karatun tanabinsa ahankali harkiran yakatse akasake kirah saiyanzu tabude idonta tadauko wayar saitaga ansa hubbina takwalalo ido tace hubbina kuma batasan harta dauki wayarba tanacewa hubbina sai asaitin kunnensa saitaji yace Na am Wata irin kunya takamata kamar tanitse cikin kasa muryarsa taji yace khadija menaji kinkirani dashi yanzu??? Duk tabi ta daburce tace dad sorry wlh banice nasakashi awayarba sahibace tasaka namanta sainakirah Ashe harnadauka kaji dakyar takeyin naganar kamar wacce akasaka dole Murmushi yadanyi maisauti yace nikuwa naji dadi danaji kinkirani hakan"" hannu tasaka tarufe fuakarta tace kayi hakuri yace aibalaifi kikayiba khadija Tace harka kaine saikuma tarufe bakinta da alamu batasan sanda maganar tafitoba"" yace ah konadawo ne bakigaji da ganinaba??? Tace sai anjima dad Dariya yayi maidan sautiii yace kunya kikejine??? Kamar yana ganinta tanoke fuska tareda daga kanta yace isowata kenan harzan soma aiki nacebari nafarajin muryarki"" murmushi tayi tace tokayi aikinka lafiya dad "mungode batajirah mezaiceba taka she wayar"" yabi wayar dakallo yayi murmushi Khadija sunagama wayar wani farincikine yalullubeta marar misaltuwa tadade tanajin soyyarsa cikin ranta Allah yakaddara shine mijinta Kullum Usman saiyakirah khadija Amman baitaba kiranta idan haryana kusa da lubabatu Sam batasan meyake faruwaba tsayin sati daya sannan yakoma kano yasanarda malam garba khadija ta amince.. Yace shikenan yabashi kwana biyu zaikirah muktar yasanardashi komai yace saiya fadamashi"" hakan kuwa akayi bayan kwana biyu yakirah muktar. Tana fara ringing yadauka tareda sallama malam garba ya amsa muktar yace kawu inawuni yace lafiya kalau ya karatu Muktar yace karatu Alhandulillah"" yace to Allah yabada sa a yabada abunda akaje nema yace ameeen muktar yace kawu ina sapna??? Yace kaima kasan tana islamiyya ni nadawo gidane indan watsaruwa saboda zafie Muktar yace kagaidamun inna " yace tana amsawa" daganan saikuma shiru yabiyo baya muktar takawarda shi run yace kawu ko akwai maganane??? Yanisa ah kam muktar akwai magana mai mahimmanci akan khadija shine dalilinda yasakama nakiraka"" jinya ambaci khadija yasaka yasaka muktar yabar abunda yakeyi yatattara hankalinsa duka yana saurarenshi Yace inajinka Allah yasadai lafiya yace qalaune insha Allah yayidan jinkiri sannan yace watarana ina kasuwa saiga mahaifin Kawar khadija labila kaganeta aiko??? Cikin kosawa yajimeyafaru yace ah nagane" yacigaba yazone akan batun khadijar daganan yakwashe abunda sukai dashi yafadamsa haryanda sukai da khadija tace ta amince Yana rufe bakinsa muktar yamike tsaye yace ai wannan zancen banzane kawu nawa khadija take dahartasan wata Abu wai soyayya bazata aureshiba!!! Kawu yace dakata muktar baikamata kahana yarinyar nan cika alkawarinda tadaukarwa kawartaba"" tace daina maganar wani alkwari kawu kawai kacemasa auren nan bazai yiyuba yayanta yace bayaso Idankuma bazaku iyah sanardashiba nimai iyah fadamasane haba kwata kwata nawa khadijar take 18years fa" Kuma tarasa wazataso sai Wanda yakeda mata !! Never Malam garba yanisa yace tonidai bansan yazanyi makaba Amman gaskiya zak asani jinkunyar bawan Allah nan tundaga kano yataso Muktar yace Allah yasa daga saudiya yazo kawu ban yarda Kanwata ta auri mai mataba!! Malam yace to Allah yakyauta sai anjima Yakashe wayar yanakallon innah yace Dama hakan nayiwagudu shiyasa nacemasa yabari saina sanarda yayanta Kinji yanda yaceko??? Innah tace lallashinsa zakayi ai saiyayi hakuri Amman magana tagaskiya yarinyar nan tanasonsa "" ninalurah dahakan tunkafin yace yanasonta Malam yayi shiru yana nazari cenyanisa yace to tundashi yakeda kanwarsa yace bayaso ahakurah mana nibanaso inyi karambani inajin tsoron maimaita tarihi duk da banada laifi Innah tace to Allah yazaba mana abunda yafi zama aikhairi malam ya amsa da Ameen bangaren muktar kuwa sunagama wayar yakasa zama jikinsa harwani ciccirah yakeyi anyama zai iyah sake kwana a kasar nan karfa yanacen kawu yayiwa khadija aure Kuma wai baban labila mai mata ai bazaitaba yiyuwaba "" dasauri yasoma hada kayanshi sai filin jirgi Koda jirginsu yasauka takwas nadare masallaci yafara zuwa yafara ramakon salloli sannan yatari Dan adaidaita zuwa gida Suna tsakar gida sunacin abinci dayake yanayin zafine saman babbar tabar marnan suke saidai sukaji sallamar sa dagasama Malam garba yadago da mamaki yana kallonsa lallai abun yayi tsamari suka amsa masa sallama yaduka yagaidasu baiko kalli gunda khadija takeba yatashi yakoma bangaren dakunansu"" yashige dakinsa Tuni murnar dakuma farincikin fuskarta yagushe takalli innah kamar zatayi kuka mikewa tayi zuwa dakin dasauri da sallama tashiga Yana kwance saman gado yakurawa silin dakin ido ahankali tataka indayake taduka muryanta tana rawa tace yaya halan bakaganniba??? Atsawace yatashi zaune yace naganki sapna mekikeso inyimaki???? Take hawaye suka jikamata fuska tace wani laifin nayimaka Yayana??? Yadallah mata harara yace kebakisan ma abunda kikaiba tunyaushe nake Jan kunnenki akan karkisake kiyi soyayya?? Asheni bansaniba ihunake bayan hari" nawakike khadija dahar zakice waikinason wani kuma bama saurayiba maimata??? Kinsan sarai natsani mai mata bazantaba bari ki auri mai mataba kodakuwa mazan duniya sunkare Tanaduke hawaye sunabin kumatunta batacemasa komaiba haryakai karshe cikin sanyin murya tace Yayana baban sahiba tane fa baikamata kajerah shi cikin sahun marasa nagartar mazajeba Yadaga mata hannu rufemun baki nalurah kedin bakida hankali tokisani gobe gobe dake zankoma sainaga karyar rashin kunya kuma shima zankirashi inji dalilinsa duk matan dasuke kasarnan yarasa wazai ce yanaso ya aurah saike zatayi magana yace kiyimun shiru tashi kibar nan banason ganinki Cikin muryar kuka tace nidin ya muktar??? Cikin tsawa yace kifita nace tsawarda yayimata cikin wata murya wacce itah kanta batasanshi da itaba Dasauri tamike tarufe bakinta saboda kuka dagudu tafita tafada dakinta saman gado takwanta tasoma kuka maicinrai meyasa nabata maka rai meyasa??? Danasan hakan zaikona makarai bazantaba bari son dad yashiga zuciyataba Su inna sai kallo kallo suke sukalli kofa sukalli juna"" sunsan koda sunshiga dakin muktar bazaitaba saurarensuba"" Dan idan yahau dokin zuciya bamai saukardashi Aisha✍🏼 ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠ chapter 73 By Gentle Lady💃🏽 Yayi shiru daga bisani yace khadija tace na am Yayana " yace kinsan bazanso abunda zai cutardake bako??? Tagyada kanta yanisa tundakike bakisan labarin mahaifiyar muba Babu Wanda tasanar mawa kisani bayanni kinada wani yayan"" dasauri tadago tace Yaya kuma a ina?? Yanisa mu uku mahaifiyar mu tahaifa Nima naji wannan ne lokacinda zamubar garin mahaifinmu tanasanarda wani malami alokacin ban fuskanci labarin sosaiba bayan nagirma nasake komawa yola Da mamaki takalleshi duk da inayaro banwani sha wahalar gane gidansaba Amman da tambaya da yake malamine sainayi dace tunda nasan unguwar awajen gwaggo hasana na tambaya Nasameshi yatsufa sosai baima ganeniba saida nayimasa bayani yanisa kwana na daya agarin hargidan mahaifinnawa natafi Amman baigane niba Naso sosai nasan inda Dan uwana yake duk Wanda natambaya saiyace babu faruq agidan malamin shine yasanardani labarinda mahaifiyarmu tasanar dashi Yanisa anan yakwashe komai yafada mata"" duk irin wahalarda tasha dayanda malamin yacemasa asirine akai mata komai baiboye mataba Yanakai karshen labarin khadija tafasheda kuka baiyi kokarin hanataba saida tayi mai isarta dankanta tashare hawayenta Yace wannan dalilinne yasaka banaso ki auri maimata Dan bazanso kema hakan tafaru dakeba"" khadija tadago jajayen idanunta takalleshi tace nagane Yayana Amman inaso kasani babu Wanda zaiwuce kaddararsa Kataba tunanin za ahaifeni???? Duk da kiyayyarda mahaifinmu yakeyiwa mamana dayake akwai rabon saina shigo duniya gashi anhaifeni Ya muktar kaddarata rubutacciyace bakada ikon sauyata inhar Allah yarubuto nima zansha wahala babu makawa hanawarka bazai kareni dakomaiba"" Kataba tunanin zan iya auren marar matar dagabaya yasake aurowata wacce zatayi nasanin fitana gidan??? Shifa Allah ba aimasa wayo baka isah ka karkare abunda yake arubuceba tunfil azal Baikamata kayiwa kowacce mace kallon hakaba Dan idanharkayi tonima wani mai irin hangenka dawannan zai kalleni Kasani ba arasa nakwarai acikin al ummah komai lalacewar zamani zakasamu akwai nagartattuñ mutane acikinsu Tanisa abunda kawai yakamata kayi kace Allah yakare maka kanwarka daga fadawa hannun irin wadan nan azzaluman matan"" kuma kabawa kanwarka makami wato ilimin Islam Wanda kowayake takama dashi Dashi zata iyah kare kanta Allah yashiga tsakaninta damiyagun mutane kumani bana zargin mom wlh baruwanta halinsu daya da labila Idanhar tanada wani mugun hali da awajen yarta zamugani Dan duk Wanda yatsotsi nono bazai yarba kamar yanda naji anafada Nikuwa nace wannan zancen burr ne inji tusa saunawa uwa take haihuwar Yaya Amman babu Wanda yagadota wani lokacin maishegen fada saita haifi salihar yarinya Wani lokacin saliha saita haifi masifaffiya danhaka masucewa waisu bazasu auri yayan masifaffuba bawai halin uwar zaku dubaba nayar dankowa da halinsa Muktar yanisa yana kallon agogon hannunsa yace dare yayi kikwanta kihuta"" kai tagyadamasa tace nagode kaima kasamu kakwanta nasan jiya bakai barciba Murmushi yasaki maidan sautii yace ya akai kikasan banyi barciba??? Itama murmushin tayi tace gashinan inagani a idanuwanka Yamike yadauko mata maganinta yace aikece kikajamun kinfita kina kuka badole hankalina yatashiba""" tace ayimun afuwa duk laifin nan dai nawane baice komaiba yabata maganin tasha yayi mata saida safe yakoma dakinsa yadade yaana nazarin maganganunta kafin yayi alwala yana sanarda Allah yazabawa kanwarsa abunda yafizama alkhairi arayuwarta Washe gari dasafe yana dakinta zaune suna firah saiga wayarta tasoma ringing jikinta yasoma rawa dantasan shine jiya silent tasaka wayar bayan fitar muktar tadauko wajen miss call ashirin tayi mamaki sosai"" saitacireta silent saiyanzu gashi yakirah Tanakallon wayar tana kallon yayanta yalurah da itah saiyashare yace wayar waye take ringing tsuru tayi alamun rashin gaskiya tace dama dama wayar sahibace tamanta da itah Dakagan yanda take magana. Kasan batada gaskiya yayi murmushi yace tokidauka kice batakusa dawayar mana"" tadan sosa kanta tace ah ah kawai barta idan yagaji zaidaina kirah kowaye Wayar hartakatse akasake kirah muktar yamika hannu yadauko wayar yaduba hubbina yaga anrubuta yadaga ido yakalleta saita done kanta yace kinganima inaganin kamar saurayintane yake kirah Shirudai tayi batace komaiba hartakusa katsewa yadauka tareda sallama dayan bangaren aka amsa "" yace barka dasafiya yace yauwa Dan Allah Khadija nake nema Muktar yadaga kai sukasake yin ido hudu tasosa kanta kamar wacce zatayi kuka"" yace togata nan tafe yakashe wayar baiko kalletaba yafita rike dawayar Jikin khadija Yakama rawa tace yaunabani mekuma yakawoshi yanxu??? Saileken kofa takeyi"" Muktar da murmushi kwance afuskarsa yakarasa wajenda Usman yake tundaga nesa yaga matukar kamarda sukeyi da labila kuma tamkarma bai isah haihuwartaba"" Shima yana ganinsa yasaki fara a kafin yakawo inda yake haryasameshi yabashiy hannu suka gaisa "" daganan suka karasa kusa da motarsa Suka sake gaisawa yace yan america saukar yaushe bayan malam yacemun bakanan"" sosai Usman yayiwa muktar kwarjini a ido Sam yakasa daga idonsa sama yakalleshi"" Yace shekaranjiya nazo"" yace toya hanya inafatar dai lafiya?? Yace ah lafiya kawune yakirani yasanardani sakonka Usman yatari nunfashinsa yace Allah yasadai yayan namu ya amince"??? Wata kunyace ta sake kama muktar yace ah gaskiya lokacinda naji Sam banyi Na am ba dalilinda yasaka nataso aranar kenan Nazone daniyar natafi da itah dankawai nace banyardaba saiyarinya tazubemun balafiya jiyama saida tasha allurah Usman yace subhanalillahi yayanmu meyasa zakaimana haka Muktar yace dad inada nawa dalilin saboda nayi alkawarin Kanwata bazata auri Wanda yakeda mataba saboda shine silar dayasa mukarasa mahaifiyar mu yanisa Amman sapna tayimun gamsasshen bayani kuma nayarda dahakan yanzu danaganka yasake nisawa yadago yakalli Usman kamar zaiyi kuka yace wlh inason Kanwata sosai itace kawai take debemun kewar mahaifiyarmu Banaso tashiga tashin hankali da matsatsin rayuwa" yasanne kansa nidama banda natauyemata hakkinta bazantaba bari tayi aureba Danba zanso wani yacutarda itaba"" Usman yamurmusa yadafa kafadarsa yace nagane abunda kakenufi kuma nagamsu nayimaka alkawarin babu abunda zaisameta inasonta sosai bawai son wasaba dasanina kaima kasan bazantaba bari wani yacutarda itah ba Muktar yanisa shikenan Allah yazaba mana abunda yafizama alkhairi usman yace Ameen"" muktar yace bari nakiramaka itah Yayi maganar yanashirin juyawa Usman yasake basa hannu suka gaisa sannan yawuce aransa yanacewa ashedai baban labila haka yake bashida girman kai"" Usman kanshi yaga saukin kan muktar"" yanashiga gidan innah tace wai inakaje naga khadija sai tsautsauniya take"" murmushi yayi yace innah dadyn labila ne yazo"" yayi maganar yana shiga dakin yace kishirya yana jiranki ya ajemata wayar akan dago harzaifita tace Yayana tsayawa yayi batareda yajiyoba tace nidai banason fita bakafadamashi gobe zamutafi dakaiba Adarare takeyin maganar yajuyo dafuskarsa wajenta dauke da murmushi yace inazanje dake kiyitamun kuka ainalurah soyayyarku hartayi nisako Tace wlh ah ah ya muktar yace hakane shiyasa naga kinyi serving din numbersa da hubbina Kafin tace wlh banice nasaba yace karkibata masa lokaci yanajiranki Amman karkidade yawuce abunsa"" murmushi tayi mayafinta kawai tadauko tasaka tasa talkamanta tafito tana leke waiko zataga ya muktar innakuwa sai dariya takemata Tafito dasauri tafita"" tunda yahangota yasoma aikomata dawani kyakkyawan murmushi Wanda itakanta bazata iyah daukarsaba akarancin shekarunta jitayima kamar kafafuwanta suna hardemata tuni tasanne kanta kasa Aisha✍🏼 ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠ Chapter 74 By Gentle Lady💃🏽 Ahankali tataka harzuwa wajenda yake tsaye shikuwa haryanzu baidauke idonsa daga kantaba tafiyarta tamkar dawisu natsuwarta kalamanta komai natadai yana matukar burgeshi Ko amafarki baitaba tunanin wai zaitaba soyayya dawataba saigashi kwatsam ya afka kogin so kuma yayi nitso tayanda baxai iyah fitaba Da tsadadden murmushinta Wanda yake matukar dimautarda Usman tayi sallama dakyar ya tattaro sauran natsuwarsa wajen amsa mata sallamarta Tace inawuni dad"" yadan gyara tsayuwa sanann yace lafiya qalau mom" dasauri tadago takalleshi batareda tayi maganaba"" yadaga mata gira yace yes indai bazaki kirani Usman ba nikuma mom zandinga kiranki dashi Bakinta tadafe 🙊Dan Allah dad karufamun asiri dawanne bakin zankiraka aikuwa danayi rashin kunya takai karshen maganar tana kallon kasa Murmushi yayi maidan sautii yasake gyara tsayuwarsa yace yayammu yace bakida lfy??? Kaita gyadamasa yace shine jiya akaki daga wayata wlh duk hankalina yatashi inata tunanin kobabu lafiya Shiru tayi cikin tsokana yace khadija meyake damunki?? Shiru taimasa saida yasake tambayarta tace bakomaifa dad Yace badaikiso insani ai yayanmu yafadamun"" baima karasa rufe bakinba tace nashiga uku mekuma yafadamaka??? Yanda tayi maganar tanaware ido tayi matukar burge Usman yasoma dariya haryana tafawa"" ido takuramasa talangwashe kai sai murmushi takeyi gaskiya dad kyakkyawane inama nice yafara aure danasan nahuce takaicin soyayya indai nasameshi Yatsagaita da dariyar yana kallonta Sam batasanma yana kallontaba saida yakada yatsunsa sukai kara sannan tadan zaburah Tanoke kanta tana Sosa kai alamar jinkunya sosai taji kunya dayakamata haka tana kallonsa"" Murmushi ya sakeyi yace toyajikin naki inafatardai kinji sauki??? Tasake gyada kanta yalurah sosai khadija tanada matukar kunya "" ganin firar tasu kamar atakure take saiyace tunda batada lafiya takoma gida shizai wuce wajen hajiya Tace masa to Allah yakiyaye hanya"" tawuce gidan tsaye yake yana kallonta harta shige "" yasaukarda sassanyar ajiyar zuciya"" motarsa yabude yadauko siyayyarda yayi mata yabawa yaro yashigar matadasu Yashiga motar sa yawuce "" koda yashiga gidan hajiya lokacin suke break yana yin sallama abdulmajeed yataso dasauri yarungumeshi yana gaidashi Yashafa kansa cikin fara a yace katashi lafiya??? Kaiyagyada masa yace Amman jiya Anty saida akamata allurah yace dagaske?? Amman ba afadamun ba Yayi maganar yana karasawa saman dinner yagaida hajiya ta amsa cikin sakin fuska labila ma tagaidashi ya amsa yayimata yajiki tace taji sauki sosai"" dama bawani ciwo bane hajiyace tatashi hankalinta hajiya tace yaunaji lalata nicema natashi hankalin nawa bayan kukanda kikaitayi kinacewa akiramaki dad"" dariya labila tayi tace aini bansan Yar tsohuwar nan tanasonaba sai ranar"" Abdul majeed yace tafisona danni idan nagirma mota zansiya mata!" Suka kwashe da dariya labila tace sannu sarkin soyayya kaikuma mezakayi da tsohuwa??? Kowa yana yayin sabon jinie ??? Yace nidai inason abuta tunda tanafita dani unguwa"" sukasake darawa "" hajiya tace kai maigidana kyaleta zauna kaci abincinka"" karka makara kara labila sai anjima kadan zata tafi"" Usman yace tonima asammun abincin banci komaiba wlh anayin sallar asuba nataso"" labilace tasoma zubamasa "" Hajiya tace kaikuma lafiyarka wannan uban sammako??? Yakarbi cup din tea daga hannun labila yace hajiya wannan tambaya hakafa??? mutum yanada uwa sukutum agari atambayeshi danyayi sammako danyaganta"" Konayi laifine yayi maganar yana kallon labila tace inafa laifi dadyna ai zumuncine kasamu lada maitarin yawa Hajiya tamere baki tace saikuje kufadawa wani badai niba kadaisan abunda yakawoka"" 'Usman yakurba tea yana dariya ciki ciki yace hajiya gaskiyar kenan Yajuya wajen Abdul majeed kaiyi sauri kashanye inkaika dagacen inwuce yau wlh aikine dani office din nan"" hajiyadai batace komaiba"" Labila tace dad bazakaje wajen sahiba taba batada lafiya"fa" ashagwabe tayi maganar abdul yayi kududum yace me dady zaiyi wajen kawarki Yakalli Usman yace nima jiya ai abokina baida lafiya Amman bakaje ganinsaba sai Kawar Anty"" kamar zaiyi kuka"" Usman yashafa kansa yace aibaka fadamunba danaje ko yarona maza dauko jakarka muje"" Abdul majeed yaruga shikuma yamike Labila tabishi da kallo tace kai daddy yanzun bazakaba kabari driver yakaishi mana kaisaikaje"" yakalleta yana murmushi yace Ashe yayanta yazo??? Tace yakirakane""" daidai fitowar Abdul yamikamasa jakar yagoyamashi itah yace cen nafara zuwa ai"" yakai karshen maganar yana kallon hajiya takasan ido yana dariya kasa kasa Murmushi kawai tayi tana girgiza kai yace mujeko nagoyamaka"" yarike hannunsa mujeto daddy"" yace haba Abdul aikanajirah nagama magana da hajiyata ko Yakalloshi da sauri hajiyarka??? Wlh hajiyatace"" yace najito hajiyarka"" yayimasu sai anjima sukai masa Allah yakiyaye yawuce yana dariyar Abdul majeed Da dare muktar yasanarda kawu ya amince khadija ta auri dadyn labila bakaramin jindadi yayiba""" yayita sakamasa albarka washe gari Yakama hanyarsa yakoma skull Usman yanadan zuwa kano akai akai"" haryanzu uwar gayyar batasanda komaiba gefe daya sunfara zana jarabar karewa balaifi sunawaya duk da haryanzu batasakin jiki suyi firah"" Usman yaturoda magabatanshi anzauna akayanka sadaki yabiya ansaka rana wata biyu"" kenan bayan sati biyu da kammala jarabawarsu Aisha✍🏼 Copied By HAYATU BABA ZUBAIRU (admin Arewa hausa novels Novels villa Duniyan novels Hayat hausa novels Hausa novels and fashion And Cool novel, makeup and cooking) WHATSAPP NO: +2347039625239 ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠ Chapter 76 By Gentle Lady💃🏽 Bayan motar tatsaya inda ake ajiyeta driver yafito yabude masa kofa Amman Sam hankalinsa baya jikinsa" saida yakirah sunansa sannan yafarga"" Yadan murja idon sa kamar Wanda yayi barcii"" dauko kayansa yayi da card din yama driver saida safe"" yawuce cikin gida jiki asanyaye Koda yashiga bata falon kasa yasaukarda wata gajiyayyar ajiyar zuciya"" Allah yasama tayi barci sai inbari saigobe nikuwa abun ma dariya yabani to aikogoben kafada abunda kake gudu zaifaru bafasashi za aiba kaidai kawai kafada musam makomarmu Ahankali yasoma hawan step din baima tsaya hawan na uraba zuwa sama tadaukeshi tsawon lokaci kafin yakai"" bangarensa yanakaiwa lubabatu tana kawowa dantayi mamaki yau yadawo dawuri Dan tunda yahadu da khadija baya dawowa saiwajen karfe Tara alokacinne yake kiranta danbadama yayi agaban uwarguba! Au sorry🙊 uwargida tunda labila tace basuyardaba tasanie Yana ganinta yatattaro sauran natsuwarsa yasamu yasakar mata lallausan murmushi itama tamiyar masa da martanin murmushinsa """ Tace sannu dazuwa yauwa yagidan yyi maganar yana turah kofar dakinsa tabishi abaya "" tace gida saitarin kadaici ai kwanan nan nakeson naje yawon kasa dani da su sajida"" yace ko??? Tace eh yamere baki baice komaiba Tace bakace komaiba"" yana rage kayan jikinsa yace Toni menene nawa ??? Da inaso dabanaso inhar kinaso saikinyi ra ayinki nasanma kina fadamunne dankar naga bakyanan Amman banda haka watarana aisaidai nabuda ido bangankiba"""" Maganarsa saima tabata dariya ganin tana dariya kamar wacce kare yaciza yakalleta baki bude yace wannan dariyar haka kumafa??? Tatsagaita da dariyar tace tomekuma nayi dankawai nayi dariya??? Yace bakiyi komaiba Amman kisani ire iren wan nan dariyar batada kyau acikin addini manzon Allah yace tana kashe zuciya tanakuma rage imani" jibifa harda hawaye kike shaidanne yakee irin wan nan dariyar""" Take annurin fuskar lubcy yagushe tace kana nufin nidin shaidance???? Yakwalalo ido yace wani banfadaba baza aji mutuwar sarki abakinaba"" Karki karagaba kifada Allah yabaki hakuri bahakan nake nufiba yadauki towel dinsa yashige bandaki yarufo kofa anan yabarta sai nanata maganarsa take aranta Haryafito batako motsaba""" yana taje sumar kansa' yadan kalleta tajikin miro yaga yanayinta yasauya"" takowa yayi kusa da itah yazauna yana kallonta yace uwargidan Usman badai maganar da nayi dazuce tasosa rankiba???? Saurin kawarda damuwarta tayi takirkiro murmushi la bakomai dankawai kasanarda ni gaskiya dannakiyaye gaba Aini nagode Allah dayahadani dimiji irinka wasu mazan zasuga matansu suna aikata badaidaiba Amman saisu kyalesu kodan kada ran matar yabaci kodan wani Abu Tace nagode kashirya abincinka yana jiranka"""yamike bari nashirya amma kafin Naci abinci akwai wani albishir dazan baki Nantake lubabatu tawashe baki tace toshikenan bari nakawo abincin nan"" tayi maganar tana mikewa tasauka waje bayan yashirya yazauna jiranta saigashi tashigo dauke da tiren abincin ta aje kasa""" cikin zumudi tacemasa tofadamun""" Yace yanzu kuwa"" hannunta yajawo zuwa saman gadon yace zauna bamusu kuwa tazauna""yana fuskan tarta yace albishirinki Tace goro fari kalkal"" ya murmusa Usman dinki yasamu wacce zai aurah!!! Kamar saukar aradu haka taji maganar batayi saurin saita natsuwarta ba cikin tashin hankali Wanda batasan yabayyana afuskar taba tace ban ban banfahimcekaba wane Usman din???? Yace kinada wani Usman dinne bayan wannan Wanda yake gabanki??? yakalleta damamaki ganin yanda har idonta yasauya"" yace yadai lubabatu kobakiji dadin furucinaba ne??? Kefa kike matsamun kullum akan nanemi mata na aurah inaki kinmanta harfushi kikeyi idan nace nida aure har abada yalokaci daya nafadamaki abunda nai tunanin zaisanyaki nishadi saikuma naga sabanin hakan??? Saiyanzu lubabatu tasan taso tabka kuskure dayake yarduniyace ta iyah tsara magana "" tayi saurin boye damuwarta takirkiro murmushi tace wlh nafika jindadin wannan ranar abunda yasa kaga nashiga damuwa inatausayin Kane dakuma kaina danakasa biyawa mijina da bukatarsa tsayin shekaru Tanisa inajin tsoron Karka auro wacce zatazo ta tayarmaka da hankali narantse danaga tashin hankalinka nagwammace naga mutuwata!!!! Wani dadine ya lullube Usman baisan sanda yamannata jikinsaba yana sakamata albarka"" tace bakomai dadyn Abdul"" nidai fatana Allah yabaka wacce zatadauki nauyin lalurarka kamar yanda kakeso Allah yabaka tagarii yace ameeen ameeen kamardai yanda yabani ke Ta murmusa wanne gari yarinyar take??? batareda fargabar komaiba yacemata kano"" aranta tace munafuki 🙄yanzu dama zuwanda yake kano soyayya yake"" kafin tatambayi sunanta yacigaba sunanta khadija marainiyace tace Allah sarki Allah yajikan iyaye yace Ameen jiki asanyaye Tace inafatardai yan uwanta sunyarda dankar ayimana kamar nasauran dakanema saimunsarai da aure saikuma Abu ya lalace"" Yace ah ah sukam bazasuyi hakaba"" kafin tayi magana yadauko card din duka yamika mata yanacewa sauran kwana biyar daurin auren Saura kadan lubabatu takundumo ashar"" takarbi card din jikinta harrawa yakeyi takurawa card din ido kamar maisabuwar makanta""" Ga rubutu nan taryen taryen takaici baibarta karasa karantawaba"" tamika masa " Yace harkin kare??? Tace ah Allah yasanya alkhairi yace Ameen"" yakarbi katin"" Yace saikiyi list din abunda kikeso duka zanje dakaina insiyomaki"" dakayan dazakici biki"" tace habadai dawainiyar tayi yawa ai" gana fatenda amare zasuyi kuma gahidimarsu aisaina karamaka nauyi Nadaigode babu abunda nanema narasa agidan nan"" yamurmusa nasanda haka Amman nasan baxaki rasa abunda kikesoba Tace wlh bakomai saidai kayanda kawai za a baiwa yanbiki""" yamike daga saman gadon yace barma maganarsu nidagayau nakashe taron biki agidana Damacen banaso Dan bidia ce kece kike kafewa saikinyi kuma dagakarshe kafin awatse sai anyimaki sata kidawo kinafada bance kigayyaci kowaba Idankuma Mace takawo kanta nasa aka koreta karkiga laifina Tace waishi wannan wanne irin tsarine yazodashi meyake nufi dahakan??? Ko anyisata aini akaiwa bashiba Yazauna yasoma cin abincinsa baidamu data yardaba kobata yardaba danshi yasan matakinda zaidauka maigadi zaifadawa karyabar kowa yashiga gidan koda kuwa lubabatu ce tazo dakanta Haryagama cin abinsa tana zaune saida yagama tamike zatadauki kayan yace xakidawo ko??? Tace meyafaru kana bukatar wani abune??? Yalangwashe kai kamar karamin yaro yalumshe ido yabude alamar ah"" Murmushi tayi tace tome kakeso??? Yace goron albishir dina mana"" kuma kinsan abunda nafi bukata ayanzu"" tagane inda maganarsa tadosa tace ayya gashi inafashin sallah""" yace kash!!! Tokitaimaka koyan dubarune kiyimun Dan Allah""" Tace please baban Abdul wlh harda Dan zazzabi nakeji kafin zuwankane nadansha maganie kabari basaura kwana biyarba aini namatsuma amaryar nan tazo nahuta Yayi dariya lallaima matar nan watakan harma gajiya kikai dani saikace wani maye"""😾 tana dariya itama tace kafadi sunanka aikai mayene Amman bamaicin mutaneba mayen........😂😂😂 Bata karasaba tasoma dariya yace najidai Amman babu Wanda yasan dahakan saike bayanke bawanda zaiganni yace inada lalurah saifa idan kece kika sanarda kawayenki Tarike baki waceni dazanbude sirrina agun wasu banzayen kawaye"" ai idan nafada watama saita kwacemun kai""" yace kedai fadi ainasan kumata tunaninku ragaggene dazaran kunhadu waku waku mata zakuta bararda zance Kuyita fadin sirrin mijinku mijinki koda katuwar loma yake wajen cin abinci baidace wata tasan yanda yakecin abinciba Shimadayake bakomaiba ballantana abunda akeso yatsaya dagake saishi waihar kina iyah sanarda wasu kawayenki bakyako jin kunya waike wautarki aimatane yan uwanki Allah yasanda hakan Amman ya la anci matarda take barbada sirrin mijinta gawasu mutanen"" haba Yar uwa lubabatu ma tasanda haka tana boyewa bata taba sanarda kawayentaba toballaike wacce bahalinku daya da lubabatu ba Kodai kiyarda dahakan kidaina fadawa kowa sirrin mijinki kokuma muce lubabatu ma tafiki wlh"" karkimanta anason mace maikunya Duk matarda batada kunya da itah da dabbobi daya saboda sune suke yawo tsirara suyi komai agaban kowa basajin kunya Aisha✍🏼 ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠ chapter 75 By Gentle Lady💃🏽 Ranadai akace bata karya saidai uwar diya taji kunya"" komai nisan dare gari zaiwaye watarana jariri zaizama ango koba hakaba??? 🤔 Su khadija sun kammala jarabawar su cikin sa a Usman dakansa yahado mata kayan lefe Amman baizo dashi gidan ba ranarda yadawo Dubai gidan hajiya yasauka anan yabar kayan Saida yasake kwana sannan yakoma kaduna"" hajiya dakanta tasamu wasu makota aka kai kayan lefen tareda labila Dan itah hannu biyuce tana wajen dad kuma tanawajen kawarta Kayanda aka tirkawa khadija kainiban taba ganin lefenda yayi yawansa dakuma kyansaba komai akwai aciki babuce kawai babu kananun kaya kuwa gasunan kamar kazanta"" nikuwa nace sa kananan kaya aisai khadija Amman su agwagwa koda sun saka jemewa zasuyi baridai kartajiyoni🙆🏿 Komai nacikin lefen dakagansu kasan sundace dawacce akasiya dominta""" labila taji dadi dangodiyar da taiwa dadynta tamkarma itace aka kawowa kayan"" masu ganin lefe kowa yazo saiyarike baki bangaren awarwaro dakuma kayan kwalliya abunsai Wanda yaganie masu karatu nabarmaku wannan aranku kukiyasta yanda kayan zasu kasance Danni idan nace zantsaya fadinsu bashakka zankwana ina bayyanamaku kyan kayan Amman bangamaba dannikaina kayan sun matukar burgeni kamardai ace lubcy tagansu wink😜 Yanganin lefe dayan tsegumi hade dayan gulma duka sungama gani sunkama gabansu""" gwaggo husaina ce tadauki nauyin dauko maigyaran jiki asoma gyaramasu Yar su Tunranarda aka kawo lefe tadauketa itama labila takwashe kayanta takoma gidan gwaggo Husaina danbataso tayi nisa da sahibarta Zuwan Usman biyu Amman baya ganinta Dan gwaggo Husaina tahanata fita ko ina"" saidai labila takezuwa idan sakone takarbo yanason ganinta sosai Amman yazaiyi Saidai suyi waya kuma batawani magana musamman idan labila tanakusa saitayita zungurarta""" yauma suna zaune an dama mata gumba tanasha labila tanagefe tana game jefi jefi tanayi mata mita waime takejirah haryanzu batashanye ba kinsanfa akwai wani tsimin yanajiranki Ta wullamata harara kamar tayi kuka tace wlh sahiba bakyasona kinsan kuwa yanda abun nan yake??? Ta aje wayar tana kallonta tace so kai aibandama karnayi barin baki sainace nafi dadyna sonki wlh Sahiba nasan zakice badadi ko??? Aibarashin dadinsa zaki dubaba amfaninda zaimaki"" tundahar gwaggo tabaki nasan yanada amfani shan nashi awajenki tagyara zama kenifa sonake kisiye zuciyarsa banaso yasake kallon kowa agabansa faceke Takarasa maganar tana dariya Khadija takaimata duka tagoce tana dariya""" khadija tace waike meyasa kike hakane kokadan ke bakyataya mom dina kishi"" Labila tace kishinme ai itah batada kishi kinga mukuwa munadashi Dan Munasonsa fiye da kammu"" itah dai labila tasan inda maganganunta suka dosa sautari tanayin nazarin hakan cewa mahaifiyarta batason dadynta dakuwa tanasonsa bazata taba cutardashiba Kodakuwa taga abun cutarwa zata iyah taremasa karyasameshi danhaka tuni tacire lubabatu cikin sahun masoyan Usman tajerata acikin makiyansa Sukuma wautarta sukegani kodan bata tashi hannun mom dintaba shiyasa batajin haushi"" kowanne da abunda yake sakawa aransa Wayar khadija ce tasoma ringing"" gabadaya suka maida hankalinsu"" wajenda wayar take kara"" my everything sukagani rubuce akan fuskar wayar Khadija ta harari labila tace aitunranar naso nayimaki magana"" labila tace to aiyanzu kinyi kidauka kartatsinke""" kuma kifadamasa munazuba idofa haryanzu baikawo mana invitation ba"" Khadija tawaro ido🙄🙄 tace nicema zanfada ??? Wlh saidaikuwà kar agayyaci kowa damadai walima kawai zamuyi koda baki kyafada Kafin tagama maganar harkiran yakatse wani yasake shigowa Labila tace kidauka mana karta katse""" saida tasake ballamata harara sannan tadauki wayar tadauka takara akunne tareda sallama"" daya bangaren aka amsa kema amincin Allah ya tabbata agareki ma abociya kyakkyawar fuska" Wani farda ido tayi""" bakisake kafin tayi magana yace amaryata kina wani abune??? Tadaga kai takalli labila sannan tagirgiza kai"" kamar yana ganinta Saida yasake tambayarta sanann tace ah ah maganar kanta tamkar tanayimata wuya"" gabadaya muryanta takashe masa jiki"" yace khadija maganar invitation dinku"" naturo akawo maki dan gaskiya bazansamu damar shigowa gobe ba aiki yayimun yawa"" cen kasan makoshi ta amsa dato"" yace hmm yanzu hardake wajen yimun rowar ganin kyakkyawan murmushinki Dariya tadanyi marar sauti tace yihakuri wlh balaifina bane "" yasake gyara zama danyanajin dadin muryanta "" yace towaye??? Taballawa labila harara tace sahiba ce"" labila tayi saurin rufemata baki"" tanagirgiza kai"" yace labilar ko"" Deejaarh! Aranta tace ya salam talumshe idonta yanayin yanda yakirah sunanta yasaukarmata dawata muguwar kasala"" cikin sanyi murya tace umm Yace Amman deejaarh meyasa zaki biyemasu kinkuwasan halinda nashiga narashin ganinki??? Wlh jinakeyi kamar zanmutu kinkuwaji yanda kirjina yake bugawa dakina kusadani dazakijiwo sautinsa"" Idanuwanta alumshe suke maganganunsa sunashiga cikin kofofin jininta"" jintayi shiru yasaka yace Deejarh"" sannu ahankali tabude idonta tadorasu akan labila anya dad yasan metakeji idan yakirata da wannan sunan Jitakeyi aduniya kaf babu Wanda yafishi iyah kiran sunanta "" yasake kiran sunanta cikin wani salon murya Wanda shikanshi baisan yanada itah ba"" tabangaren Usman idanuwansa harsun rikide saboda chananin sha awarda take damunsa kwana shidan dasuka rage bikinsu ganiyake tamkarma shekara shidane Saiyaga lokaci yadaina gudu kwanaki ganinta yakandan ragemasa damuwa Amman yanzu tsawon wata dasati uku baisakata"" a idonsaba saidai kawai awaya kuma koshi batadauka saitajamasa rai kokuma duk kunyace Yacigaba please Deejarh kitaimaka zanzo gobe saikifito naganki koda bazaki dadeba"" aranta tace nima inason ganinka"" dad inajima kamar nayi kuka rashin ganinka"" jinshirun yayi tsayi yace Deejarh bakice komaiba idan bazansamu ganinkiba kidaure kifurtamun kalmarda zata ragemun kewarki""" tsuru tayi kamar wacce tai karya "" yace kobaxaki iyah ba??? Tace nifa dad kunya nakeji"" labila mikewa tayi tarankwashe ta akai tafita dagudu"" saida khadija tasaki kara Dasauri Usman yamike yana tambayarta lafiya??? Tayisaurin saita kanta bakomai kafata nadanbuge"" yace ayya sannu amaryata Kunya takeji idan yanakiranta dawan nan sunan"" hannutasaka tarufe fuskarta"" yace yadai amaryata kunya kikejine??? Tace umm tanagyada kai Yace ainakusa rabaki dawan nan kunyar"" watakunyar ce yasake jefata aciki"" yana kallon agogo yace kingama lokacin sallah yayi"" Amman bakifadamun kalma kodayaba Shiru tayi"" yace please ! Kokinaso inzo yanzu kokifada koyanzun nataho"" ido taware tace darefa yayi Yace toki fadamun"" ahankali tafurta I L O V E You Tayi saurin kashe wayar taboye kanta ajiki filo" bangaren Usman wani dadi yaji yakalli wayar yanasakin murmushi kamar yana kallon fuskar Khadija Tashi yayi yasallami ma aikatan sukayi haramar sallah"" bashi yafitoba"" sai bayan isha"" i Khadija kam tana kwance tundasuka gama waya dayake tana fashin sallah batayi yunkurin tashiba harbarci yadauketa awajen Usman ne bayan mota Muhammad yana tukashi zuwagida hannunsa katin daurin auren sune da khadija yau yakeson sanarda lubabatu maganar aurensa saboda yasan halin magulmata shiyasama baibawa kowaba danyasan muddin yarabashi tokota halin yayama saitasamu labari Jinginawa yayi jikin kujerah yalumshe idonsa tundayake baitabajin fargabar sanarda lubabatu yanason kara aureba saiyau kirjinsa saibugawa yake Sunakawo wa kofar gidan yasakejin gabansa yafadiii dasaurii yasoma furta innalillahi wa inna ilaihir rajiun حسبنا الله ونعم الو كيل Aisha✍🏼 ☠ *HATSABIBIN BOKA!!!*☠ Chapter 78 By Gentle Lady 💃🏽 Yasake kecewa da dariya yace yakike kuka kizama jaruma mana aikinsan nibana magana biyu kijirah kafin tashigo gidan munsan yanda zamuyi ai akwai bakaken aljanu dakuma masu shan jijin bil adama Hayyanul zairi yayi tafiya kasar iraqi na aikeshi nemomun wadansu kayan danakeso nayi tsafi dasu"" zaidaukeshi tsayin wata kafin yadawo dankuwa dajinda zaishiga yanada hadarin gaske bartashi aljani saboda akwai miyagun dabbobi masu cin naman aljanu acen idankuma mutum yasake tsautsayi yakaishi cen saidai uwarsa tahaifi wani Inason Gina fadata acen saboda wani dalili"" dayana nan tuni aikinki yagama danhaka saiki jirah kafin yadawo yanakai karshen maganar yadafa tsapappen zakinsa take yabace dashi da zakin lubabatu saida tazaburah tamiyarda madubin mazauninsa Tagumi tabuga aranta tace anya wannan bokan baihada iri da aljanuba??? Nidai naga abunnashi saigaba gaba yakeyi yanzukuma waifada za aginamasa a Iraqi lallai wani Abun sai matsafa Hmmm yanzun inaji inaganidai Usman saiya auro wannan shegiyar yarinyar"" tayi shiru aikuwa inyasan wata baisan wataba bakin zuciyarsa zan kulle tayanda zaiyita masifa da mutane baburuwa koni tashafeni Amman saina lalata wannan auren badai Saurah kwana biyarba hmm ayimuganie to Mikewa tayi tabude drawer tadauko wata Yar battar karfe tafita zuwa kitchen takunna gas takara battar karfen ajikin wutar tasoma daukar zafii saida tayi zafiii rau sannan takulle bakin battar takoma daki tana murmushin mugunta Lokacinda wannan abun yafaru Usman yadade dayin barcii acikin barcinsa yasomajin ransa yabacii zunbur yamike yakalli agogon dakinsa asuba takusa tsaki yasoma yi kamar Wanda akaiwa laifi Jiyakeyi tamkar yarufe kansa daduka"" yarasa yazaiyi hannuwa yasaka yadafe kansa yanakiran innalillahi ahankali yadan samu natsuwa yasakeyin addua Yakoma yakwanta danbarci yakeji Washe gari lubabatu batamasan sanda yafitaba wajen aiki kuwa gabadaya suka rasa gane kansa koda maganar arxiki kaimasa saiyamiyar maka datatsiya Idankuma kadameshi da surutu yahauka da masifa kamardai Wanda kare yaciza yanazaune akan kujera yakurawa tarin takardunda suke gabansa ido kamar maitunanin wani Abu gabadaya jinkansa yake kamar banashiba zuciyarsa sai tururi takeyi kamar hayaki"" wayarsa yadauko yakuramata ido yaukwanansu biyu basuyi waya da khadija ba tunranarda yaji ransa yabaci yaji bayason kiranta lambar yakamo yana kallo kamar zaikirah Yacigaba da jujjuya wayar cenyadanna kirah tayita ringing hartakatse ba adaukaba nantake yaji ransa yabaci yasake kirah Khadija tana zaune tareda labila tanayin karatun suratul bakarah labila tana saurarenta saboda walimarda za aimata sai Amarya tayi karatu Shine takeson labila taduba mata duk da tasan bata mantaba wayarta tana hannun labilar sanda yakirah dayake bata ringing sosai bata daukaba.. Dakiran yasake shigowa garin takatse kiran Ashe tadauka kuma hankalinta bawajen wayar yakeba Sam batamasan tadaukaba . Shikuma usman yanaganin andauka haryabuda baki daniyar sakin magana yajiyo zazzakar muryar khadija tana karatu. Wata irin sassanyar ni imace yaji tasauka azuciyarsa tuni yanemi damuwarsa yarasa"" aitake yasoma record yasaka Hans free Idanunsa yalumshe tamkar maijin barcii harcikin kopofin jininsa muryar khadija take shiga tsayin wajen mintuna ashirin barci maidadi yayi awon gaba dashii Cen cikin barcinsa yakejin ana helo dad kanajina maryar labilace tatasheshi baimasan yayi barcinba tashi yayi"" yayimika tareda hamma lahaula walakuwati illah billah Save din recodin din yayi sanann yasake kirah danwasai yakejinsa kamar ancire masa dukkan damuwarda keransa Tanasoma ringing labila tadauka da sallama ya amsa yanasake lumshe idonsa tace dady barka dahutawa ya aikin??? Yace Alhamdulillah ina khadija??takai kallonta wajenda khadija take tace gatanan yanzun mukagama karatu zamufita raba invitation ne"" yace saiyanzu zakufara rabawa??? Tace ah ah tunjiya muka fara dare yayi saimuka dawo gida Dan akwai mutane dayawa wadanda yakamata mugayyata Yace shikenan tokarna tsaidaku saikundawo kikula kinji yarlele"" tace to daddy nagode"" yanaso yace tabawa khadija kuma yakasa danhar yanzu yanajin Dan nauyin labilar Takatsemasa tunani dacewa dad gasahibar tayi maganar tana mikamata wayar takarba itakuma tafita dantalurah inhar gabantane sahiba bata iyah wata firah dashi takara akunnenta kafin tayi magana yace amincin Allah yatabbata agareki hasken zuciyata"" wani daddadan sanyine yaratsa kofofin sadarwarda ke kaisako ga zuciyarta talunshe ido tanamai saukarda ajiyar zuciyar wacce Usman yajita Tare dakai ma aboci fara a dakwarjinie"" wani dadiyaji marar misaltuwa waima anya khadijarsace tafurta masa wannan Kalmar??? Kafin yagama tunani tace inafatar kanacikin koshin lafiya??? Sumar kansa yashafo yace INA lafiya fatar kema haka??? Tabude idonta ahankali tana kallon ko far dakin tace idan nacemaka haka nayi karya hubbyna Wayyo dadi kasheni kusan Usman sumar zaune yayi"" cikin kasalarlar murya yace meyake damunki Deejarh Na??? Tanisa akwai wani Abu dazaidameni aduniyar nan inatareda gwarzon namijie kawaidai kaunarka dakuma kewarka sune sukataru suka dameni azuciyata Harnakejima tamkar narasa wani muhimmin bangare ajikina"" yagyara zamansa yanalaso busassun labbansa haryanzu idonsa kullesuke dantsabar yanda yake jin dadin firar jiyakema tamkar asararin samaniya yake yawo Deejarh yakirah sunanta akaro nafarko ta amsa na am hubbyna"" yaja ajiyar zuciya yace waidagaske bamafarki nakeyiba??? Tarausayarda kai tace kamarya hubby ??? Yamurmusa wlh jinakeyi tamkar inawata duniyarda babuwani mahakuli acikinta face nidake bantaba tsintar kaina atsantsan soyayya irin wannan ba"" waidama haka soyake da dadi hakika nasake yarda soyayya tafi Zuma dadi inhar mafarki nakeyi banafatar nafarka daga wannan daddadan mafarkin harkarshen rayuwata Inaso incigaba dajin wadandan dadadan kalamanki sunamatukar sanyaya manie zuciya""" khadija tadan kishingida tace kokadan masoyina ba mafarki kakeyiba a farke kake kabude idonka zakaganni akusa da zuciyarka indai har kalamaina suna sanyaka nishadi nikuma bazangajiba wajen furtamaka su harsaisun cika duk wani bango dake zuciyarka Nikaina bansan soyanada dadiba saida nayidace da ma aboci soyayya irinka hakika ninasan nayi dace samunka agareni babbar nasarace inarokon Allah yasake mallakamun kai hasken zuciyata Usman bakin nanfa yakirufuwa wai Ashe Usman ya iya soyayya??? Abunda baiyiba koda budurwarsa ta mafarki yanaji ajikinsa kamar yanzune zaiyi auren soyayya Matarsa ta mafarki ya auretane saboda yanajin tausayinta akan abunda matar ubanta takemata "" haka sauran matansa daya aurah azahiri yanasonsune kawai danbukatar sha awarsa lubabatu kuwa jiyakeyi kamar adolene ya aureta Soyayya tagaskiya kuma kwaya daya tak babu macenda yadamkawa itah sai khadijar sa"" tsayin lokutanda suka dauka labila tanashigowa khadija tacemasa zasufita Yayimasu Allah yakiyaye tareda kafuzza masu dadi tanakashe wayar tadafe kirjinta labila tahauyimata dariya tace inafatardai bakimanta ko kalma dayaba Harara takaimata taçe wlh kinbani aiki sahiba bakiji kunyarda najiba"" labila tazauna tana fuskantarta tace haba khadija mijinkinefa Wanda zaki aurah wllh ajiye kunya zakiyi agefe kirungumi mijinki idankuma bakiyiba kinaji kinaganie kunya tacutardake kinga tashi muje abarwannan darasin saigobe Khadija tamike sukafita suncewa inna suntafi tayimasu adawo lafiya Aisha✍🏼 ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠ Chapter 77 By Gentle Lady💃🏽 Anason mace mai kunya hausawa sunacewa kunya adon yammata"" mace ballagaza itace batada kunya Nidai shawarda zanbaki Yar uwa inhar mijinki yazama irin haka kokuma akasin hakan kisamu kuwarware matsalarku atsakaninku batareda kunyiwa juna tonon asiriba Danwannan babu abunda yafishi zama tonon asiri "" shinwaima idan kinfadawa wata tanada maganinda. Zatabakine ??? Ninasan babu abunda zatacemaki saidai tace kiyi hakuri shine kawai Shawarda zanbayar itace idan mijinki yakasance kinkasa biyamasa bukatarsa ta auratayya tokirika hadamasa da dubaru wadanda kikasan basu sabawa addiniba zaki iyah yin koma mene danyasamu gamsuwa ajikinki saidai banda waje daya Wanda Allah yamana iyaka dashi wato bayagamutum Koya mijinki yakai kolokuwar bukata inhar yanuna maki yinhakan karkiyarda Amman bayan nan ko inane halal ne "" idankuma bukatarsa tawuce duk wata dabara dazaki masa tokibarsa yayi aure Karkuma kitada hankalinki idan kikaga ya auro wacce take iyah hakuri da bukatarsa"" karkiga laifinsa bashine yayi kansaba haka Allah yagadamar yinsa saiki tausaya masa Idankuma baida halin auren Yar uwa inkinada hali kibashi kudi yayi bawai faduwa kikaiba sakamakon aikinki yana wajen Allah" idankuma bakida hali kema tosaiki bashi shawara yarika hadawa da azzumie domin kare kansa daga fadawa ga aikata zina Manzon Allah yanacewa awani hadishi dayake kwadai tarwa akan aure" وقال صلى الله ءليه وسلم يا معشر الشباب من استطاع منكم الباءة فليتزوج فإنه أغض للبصر وأحصن للفدرخ ومن لم يستطع فعليه بالصوم فإنه وجاء رواه البخاري ومسلم manzon Allah tsira da amincin Allah sutabbata agareshi yanacewa yaku taron samari masu iko daga cikinku tosuyi aure ma ana wadanda sukeda kudin auren kuma sunkai munzalin yin auren sunada bukatar mata "" cewashi aure yanakarewa daga ganie dakuma sha awa " Wanda kuma bashida iko ma ana baida halinyin auren kokuma idan yayi auren bazai iyah daukar dukkanin hakkin matarba sai manzon Allah yace nahoreshi dayayi azumie sabodashi kariyace Wannan hadishin basamariba harmai mata zai iyah aikidashi inhar yaga yakusa fadawa ga aikata zina Yar uwa saikibashi shawara yafara azumie kema zaki iyah tayashi kinga yasamu ladabiyu galadar azumie kuma galadar kiyaye kansa dadi biyu kenan Idankuma kece dayawan bukata shikuma bayada shima zai iyah wasadake danyaragemaki kamardai shidin saikuma kikara da hakuri idankuma kinji bazaki iyaba zaikaiki ga hakala saikisameshi kuzauna kifadamasa karkiboye komai Tsakaninku kuwarware matsalarku idan baida lafiyane saiyanemi maganie idankuma haka Allah yayishi saiya sauwake maki kisamu daidaike kuyi rabuwar mutunci Amman gaskiya indai harzaki iyah hakuri tohakurin zaifi zakici ribarsa agobe kiyama Allah yasa mudace Lubabatu tace wlh bayabon kaiba nikaina idan naji masu sakin baki sunafadawa wasu matan sirrin gidajensu haushi sukeban saikuma kaga wadanda sukafisu wayo subasa fadar nasu saidai su saurari naka Usman yace aishine rashin hankalin nagode Allah da matata batacikin ire iren wadan nan matan"" nikuwa nace Allah yasa masu karatun wannan labarin basacikin wadan nan matan Idankuma kinayi tokinji dagayau saikigyara rawarki kisauya taku wadanda kuma basuyi aurenba sukiyaye dangaba yayimasu amfanie Zaki iyah turawa wata domin takaru kema kin isarda sako Allah yasa muzama masu rike sirrinmu Ameen Lubabatu tamatsu tabar dakin danfayau tashiga rudanie Tayakuna fuska nidai zankwanta kakula dakanka""" yace shikenan Allah yasauwake konazo natayaki barcin??? Tayi saurin cewa ah ah nagode nahutardakai saida safe tayi maganar tana bude kofa"" yace tosaida safe tafita taturo kofa"" wai wata sabuwa lubabatu harda gudu gudu take hadawa jitakeyi kamarma tazama iska takai kanta wajen *hatsabibin boka* tanashiga dakinta sauran kadan tafadi garin mugun saurinta"" Takulle kofa tafada dakinta wajen drawer tadauko akwatin tabude tafitoda karamin madubin sai walwalniya yakeyi tashafa cikinsa jikinta yana rawa tareda kiran sunan *hatsabibin boka* muryanta tanarawa kamar maikuka Daka ganta kasan tanacikin tashin hankali shafawarta keda wuya saiga wani duhu gabadaya ya mamaye dakin abunda bata saba ganiba gabadaya dakin yayi baki kirin wutar dakin tadauke bataganin kotafin hannunta Wani tashin hankali tasake shiga al amarinda yasoma saukarmata da faduwar gaba lallai wanann matar kilanta wajen boka takaishi shine abunda lubabatu tasoma rayawa aranta Batagama tunaniba haske yasoma samuwa acikin dakin sannu ahankali haryagama mamaye dakin saiga *hatsabibin boka* yabayyana asaman tsafaffen zakie ido hudu kawai lubabatu tayi dazakin tasaki fitsari daga zaune ganinhakan yasaka *hatsabibin boka* yatintsire da dariya kamar bazai dainaba Zuwa dakiku ashirin yatsuke fuskarsa tamkar Wanda baitaba dariyaba saiga idanuwansa masu munin gaske sunkoma koraye shar yasoma wani irin hucii kamar mesa hucinsa haryana fesowa lubabatu Cikin tashin hankali tace yakai wannan hatsabibin matsafi kasani yauban kirakaba saida mummunan labari saiga hawaye sharrr akan kumatunta suna zarya Tacigaba waini Usman zai ha inta??? Haryatashi aure baisanarda niba??? Sai anasaurah kwana biyar waiyama akai aikinda kaimasa baikama wannan shegiyar yarinyar ba Haryanxu bokan kallonta kawai yakeyi baice uffanba saida takai karshen maganarta sannan yabushe da dariya yace wannan ranar batada sa a gareki Tunkafin kisanardani gabadaya aljanuna sunce bazasu iyah jayayya dawan nan yarinyarba sanadinda yasaka kikaga batakishiba aljaninda yake yin wannan aikin yakasa shiga jikinta Hasalima yanzun yanacen yanajinya sanadin rauninda yasameshi dayaso rike hannunta"" kozaisamu kafar shiga jikinta Cikin rudani lubabatu tace nashiga uku boka wannan kuma wace irin hatsabibiyar yarinyace??? Wajen wane irin boka takaini Wanda yakeyiñ aikinda yagagari aljanunka su shafeta??? *hatsabibin boka* yasake kecewa da dariya yace nikaina yau banacikin yanayi maidadi lokacinda kika kiranie ina karkashin kurkukuna dayake kasan kasa"" ina ganawa wata aljana azaba!!! Cikin lubabatu yaduri ruwa kamar tazunduma dagudu yacigaba kirankine yasaka nahau dokina nazo gareki kisani wanann yarinyar tasha banban da irin matanda mijinki yake soyayya dasu Wannan takere duk wani tunaninki saboda hafizace kuma tanada yawan ibada narantsemaki da karfin tsafina dana gadà kaka da kakaññi babu wani aljani aduniya daya isah yatunkareta haryashiga jikinta batareda yakone kurmus ba yamutu Kebarta mutuwama ko tokarsa ba azasamuba!!! Take lubabatu tasoma yarfe zufa tace togaskiya banaso ya auri wannan yarinyar danmuddin tashigo gidana zatayi wuyar fita "" kaiyagirgiza yace babu makawa saiya aureta!!! Saidai kiyi hakuri idan akai auren kisake kirana kafin lokacin ninasan hanyarda zanbi domin mukasheta danwanann muddin tana raye tosaitaga karshenki Lubabatu tadafe kirji tace wlh saidai naga karshenta Dan ubanta tafashe dakuka"" yanzun dole saitashigo gidan??? Yace tabbas kimadaina barnar hawayenki babu abunda zai gagari *hatsabibin boka* idankuwa har akwai wani aiki dazai gagareni tonikuwa banchan chanchi akirani *hatsabibin boka* ba Kikwantarda hankalinki kamar tsumma aranda"😆😆😆" tace wane irin kwanciyar hankali zanyi bayan anashirin kawomun annoba!! Waikunjitafa🙄 wai annoba! Bayankuma itace annobar😕 Masu karatu kuyi hakuri da iyah abunda kukesamu baidace kuna rainawaba inama laifina inayin wannan kullum karfa kumanta inada aikinyi bawai zaman remote nakeyiba kurika hakuri daduk abunda kukasamu kunsan typing dinnan kansa wuyane dashiii bawai yawan typing ba Allah yasa kuna amfani da abunda kuke karantawa Idankuma kawai dannishadinku kuke karantawa babu amfanin inrika bata lokacina😒 Aisha✍🏼 ☠ *HATSABIBIN BOKA!!!*☠ Chapter 79 By Gentle Lady💃🏽 Akwana atashi hasarar mai rai yaune ake daurah auren khadija"" kawu shine yazama waliyin khadija Dan muktar yace wlh bazasu je yola ba aibadole sai anje wajensa za aiwa kanwarsa aureba tundahar yace shibayada wadansu yaya tosuma sunmanta dashi kamar yanda yamanta dasu Duk da bahakan kawu yasoba Amman yakyale babban masallacin jumua dayake kano bayan antashi sallar jumua akadaurah auren *Usman Adam yunus* & *khadija Muhammad* Akan sadaki dubu talatin kamardai yanda khadija tace akarba dan samun albarkar aure"" tunda aka daurah auren Usman yasomajin wani irin farinciki acikin ransa"" Waiyau khadija tazama mallakinsa Abdul saitsiya yakemasa danshima baya kasar yana minna dashi da iyalinsa acen yakoma dazama da iyalinsa bikinne yasa sukazo farincikinda Usman yakeciki bazai faduba mai karatu ka kwatantashi aranka"" Usman yanacikin dakakkiyar shadda fara saol tasha aikin wuta da babbar rigarsa"" takalmansa hularsa agogonda yake daure akan hannunsa komai iri dayane muktar ne tareda abokansa suka karasa sukabashi hannu sukagaisa sunatayashi murna Daurin aurensa yatara dubban jama a anci abinci tareda abubuwan sha kamar gabanza akesamosu naman kajikuwa kamar suyi magana Anagama daurin aure suka kwasa da abokansa saigidan hajiya"" huuuu nikam naceyau nasan baza agane labila ba"" Da la asar za agudanarda walima makarantarsu khadija gidan hajiya yacika da yan uwa da abokan arxiki ko inakaduba mutanene gasunan kowa kaganshi yanacikin farinciki " kubrah matazo tunjiya da faruq kubrah yayanta uku yanzu suma sungirma tubarkalla" Bari muleka gidan Amarya muganie tundaga zaure nasomajiyo kamshin turare dagaji kaima kasan hadaddiyar Amarya ce agidan waiwai masha Allah yanda naga khadija badan naganta tareda labila ba dabazan ganetaba" muktar kansa dayaganta bakinsa kinrufuwa yayi saboda ganin yanda kanwarsa takoma tamkar tauraruwa duk inda tawurga saimutane sunjuya"" tayi kyau matuka zanen lallinta yabada ma ana sosai gidayacika dayanbiki masu cinye shinkafar mutane😝 Hayaniya nasomaji awaje naduba naga kosuwaye mezanganiey😳 taron yan group din Haneefa Usman ne wato zangon labarai"" su rabie da Aisha harture fateema Ali sukeyi saboda zumudi Bayansukuma zugar su kausar luv" ne Jidda Aliyuu" Haneefa Usman" hafsat m Sharif" fateema zuhurah " fateema Shuwa"rahmaluv" naanyluv" jameela muhd Ali" Shafa atu Umar maryam Lele Style"" Aisha iliya"" Anty Jidda billy baby"" ummu fauzan " kaikai wadansu digaya Nagano sun lunka nafarkon danabiyu idan manatsaya rubuta sunansu aikuwa sai nacika safin harma inbude wani shafin🙄 Gefe guda nakoma nadauko wata takardar nasoma rubuta sunayen wadanda sukaje✍🏼 naany rabie Aisha sune nafarko sanann sauran sukabiyo baya saida nacika shafi bakwai najinjina wanann karartasu nalinke takarda Na ajeta dazaran munkai amarya zandankata gahannun lubabatu domin tayimasu kyauta maitsoka tukuicin murnarda suka tayata wacce bataji sunantaba kuma taje yawan people baisa nagantaba saitamun magana akwai sauran takarda daya😂😂 Gabadaya suncika gidan nikam nace anyakuwa wadan nan duk angayyacesu🤔 inajikamar akwai gayyar sodii labila tarasa inama zata sakasu danjin dadi takaisu babban falon gidan hajiya tajido masu abinci sukaita narkaa nikam koruwa banshaba!!😑 Baridai muleka bangaren Amarya" au sorry uwargida muga wainarda aketoyawa acen"" tunda nashigo unguwar najita tsit tamkar ba biki akeyiba nakarasa wajen maigadi domin yabudemun kofa yace alhaji Usman yace ko kuda sukazo kar abarsu sushiga harsai ankawo Amarya Nayi murmushi nace kowayacemaka??? Yace ah kowafa nace kirashidai kaji nikam nasan bazai hanani shigaba idan baniba babu mai iyah dannar kirjin lubabatu babumusu yaciro waya zaikirashi Na kaikaici idonsa nakude gidan saidai yajuyo baiganniba "" tunda nashiga gidan naji shiru nace wayyo labila tayiwa makota bakinciki dayanzu sunanan sunadibar gara Nayita kwada sallama najishiru nahaye harbangaren lubabatu tunkafin inturah kofa nakejin kukanta baki narike yaufa akeyinta uwargida nakuka Kwance take kasa sairusar kukatake takeyi tun lokacinda Usman yashirya yacemata yatafiii tayi zaune tana kallon agogo tanata addua Allah yasama yayi hadari yamutu ubankowa yàhuta Nikuwa nace cenkigani atukunyarki 😕in Allah yaso qalau zaikai tunda taji biyu tabuga tasan andaurah aikuwa tafado kasan gado tayita rusar kuka gashi Usman yahana kawayenta shigowa dansaida sukazo maigadi yace babuwacce zatashiga Saida suka kirah lubcy tazo dakanta yace ogane yabada wannan umurnin takirashi awaya yace shine yabayar dolensu suka koma tadau alwashin saitasa *hatsabibin boka* yayiwa wannan khadijar kisan gilla mutuwa mafi muni acikin kowacce kalar mutuwa Gawartama bataso asamu ballantana aimata sallah tundatake babu wacce tataba sakata adamuwa tazubarda hawayenta sama dawannan amaryar aibasaida tsafiba takissa kawaima saita fitarda itah kuma bazata huceba muddin khadija tana numfashi adoron kasa saitaga karshenta!!! Nikam bakin kofa natsaya ganin har anyi la asar nasan yanzun haka antafi walimar sallah nagabatar sannan nawuce alokacin lubabatu barcin wahala yashureta"" Harabar babbar islamiyyar tacika makil abokan kasuwancin Usman dakuma yan uwansa tarin masoya dakuma makota tarin malaman makarantar dakuma manyan malamanda aka gayyata wajen ba masaukar tsintsiya bayan anbude taro da addua akakirah Amarya labilace tatake mata baya sanye take cikin atamfa mairatsin bakii daja sai babban hijab dinta harkasa tasaka safa hannu dakafa gakuma likaf babu hanya ko daya dayayi Saura ajikinta takarasa wajen malamin takarbi lasifikar tasoma karatu gabadaya wajen yayi shiru Usman baisan sanda yafurta Alhamdulillah har takare karatu takoma mazauninta Usman baisaniba saida babban malaminsu yafara wa azi akan zamantakewar aure Aure rahamane ba karama bawani bangarene najin dadi rayuwa duk Wanda yatakashi yaji dadi sosai "" Allah ne yace ayi aure domin rahamace bakarama yayimana Allah yanacewa (فانكحو اماطاب لكم من النساء مثنى وثلاث ورباع فإن خفتم ألا تعدلوا فواحدة أوما ملكت أيمانكم) Ku auri mataye wadanda aka halartamaku aurensu daga cikinku Ku auri biyu ko uku ko hudu idankuma kunsan bazaku iyah yin adalciba atsakaninsu toku auri daya ko abunda dayanku ya mallaka ma ana kuyanga suratul nisa i domin aure yazama rahama agaremu Allah yacewa annabin rahama " (ولقد أرسلنارسلا من قبلك وخعلنا له‍م أزواجا وذرية) Mun aikoda manzanni gabaninka mukasanya mata dakuma zuria agaresu suratul ra adi Aure wata bbbar rahamace dakuma jindadin rayuwa agaremu kamar yanda Allah yakece awata aya datake cikin suratul rum (ومن آياته أن خلق لكم من أنفسكم أزواجا لتسكنوا إليه‍اوجعل بينكم مودة ورحمة إن فى ذلك لآيات لقوم يتفكرون Acikin wata aya anhalittamaku mata ku auresu domin kunatsu da itah matar kuma akasanya kauna dasoyaya atsakaninku dakuma rahama mace idan tayi aure alokacin tacika Rabin addininta sauran saitayi biyayya gamijinta yake wanann Amarya kisani aljannarki tana karkashin tafin mijinki nasihardà zanyimaki Anan shine ki kiyaye hakkokan mijinki idan kikaji ance hakki toyasafi komai dakomai abunda yarataya awuyanki ke Amarya Manzon Allah yanacewa awani hadisi" إذادعا الرجل إمرأته إلى فرشه فلم تاته لعنته‍ا الملاعكة حتى تصبح Idan miji yakira matarsa zuwaga shinfidarsa idan batazoba "" mala"iku zasuyita la antarta hargari yawaye Tokunji mata dayawa yanzukuwa masu gudun mazajensu bazasuy kirguba"" Kiyiwa mijinki biyayyya duk abunda yasaki jikinki yanarawa kije kigabardashi cikin dadin rai"" Manzon Rahma yanacewa acikin wani hadisi لوكنت آمرا أحدا أن يسجد لأحد لأمرت المرأة أن تسجد لزوجها" رواه الترمذي" Daza a umurci wani yayi sujada gawani lallai daza a umurci mace tayiwa mijinta sujada Acikin wani hadisi manzon Allah yanacewa duk matarda tafita gidan mijinta batareda izinin mujintaba tanacikin tsinuwar Allah da la antarsa hartadawo gidanta kukama tanemi yafiyar mijinta ma ana tanemi gafararsa yayafemata yake wanann Amarya nahoreki darike sirrin mijinki kisanI ke sitrace gamijinki baidace kibayyanawa wata sirrin mujinkiba koya kike da itah Kikasance mai tattausan lafazi agareshi karkisake muryarki takere tashi awajen magana karkirika magana dashi kamarwani yaronki Dan asabe nafadamaka magi yakare babu daddawa gishirima sauran nagobe haba Yar uwa ahakañ tayakikeso kisamu rahama "" kizama maikwalliya dakuma kyalkyali kullum aganki tsaf dakinkima yayita kamshii kizama maitsafta karkibar bakinki yanadoyi ansha miyar kuka tsami gaye Dan matsitsi dasauransu Ba ahanaki cinkomaiba Amman dazaran kinci lokacinda zakije bangaren maigida saiki tsabtacesu karkijemasa baki yana hamami kamar shaddar Masai Idankika gyara kekanki zakifijin dadi""kirika aske gashin gabanki dana hammata duk inda kikasan wata dauda zata makale kiwanke wlh wata saikuga gashin hammatarta kamar iccen kwakwa natabbàta wata kwararriyar maikitso zata iyah kitsashi har asamasa ribon yake wannan amarya inahoronki dakarki sake kibudabaki kicewa mijinkii yasakeki!! Manzon Allah yanacewa duk ranarda mata tacewa mijinta yasaketa batareda wañi daliliba Allah yaharamta mata jin kamshin aljanna aljannama bazataji kamshintàbà ballanta tasaran shigarta Allah yakiyashemu Aisha✍🏼 ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠ Chapter 80 By Gentle Lady💃🏽 Karkisake kibar kawarki tazauna maki kangado " gadonda mijinki yake kwanciya kuraya sunnar ma aiki wata shibgegiyar katuwa tadosana duwawunta inda yake kwanciya batako jinkunya"" inbanda lalacewar zamani mezaikaiki dakin kwanan kawarki??? Koda kinje wajenta kikwahe falo mana kofalon asamarwa maigida kujerah ta musamman ko yaranki karkibari surika zama akanta"" Haka kwanonda yakecin abinci kokuma cup dinda yakeshanruwa karkibari wata takafamiki baki inda yazamana mijinkima idan zaisha ruwa awajen zaikafa nasa yadace komai namijinki yazama dabanne danakowa Yake wannan Amarya kisani tubalinki shine gidan mijinki yadace agareki duk inda kikaje karkisaki jiki awajen face kinadakin mijinki kiji aranki koda gidankune bazaki sakeba bisaga dakinki Kizauna dayan uwansa lafiya dakuma makotanki idankinada abokiyar zama kidauketa tamkar Yar uwarki karkizama cikin sakarkarun matannan masu shegen kishin tsiya sudai bashason koya dagasu sai yayansu"" ramin kurah kenan Idan kikace haka tokinyi kamaice ceniya da kurar kenan"" kirike abubuwa guda shida wadanda zanfadamaki 1 Ibada 2 tsabta 3 iya magana 4 rike sirri 5 hakuri 6 iyah abinci Dadai sauransu inhar kika rike wadan nan zakici ribar zaman aure anan zandakata dankuwa idan nace zanfadi fa idodan aure dakuma hakkokansa zamukwana muwuni banfadi ko kwataba inayiwa wannan Amarya da agonta fatan samun zaman lafiya dakuma zuriya dayiba ma assalam Daganan yamikawa wani malami yatashi yasoma dajawabin godiya duk abunda zanfada malam yarigada ya fadeshi inarokon Allah yasa kowa yayi amfani da abunda yasaurara kuma yayi aiki dashi "" Ameen munayiwa dalibarmu kuma malamarmu fatan samun zaman lafiya dakuma kwanciyar hankali agidan mijinta Allah yasa ace kara da akayi Allah yakauda fitinardake tsakaninsu Allah kakore shaidan atsakaninsu Allah yabasu Yaya nagari " Subhana kallahumma wabihamdika ash"hadu anla ilaha illah anta astagfiruka wa atubu ilaika Daganan akabaiwa wani malamin yabude taro da addua"" akasoma raba takeaway"" kowa Yakama gabansa saifatan Allah yabasu zaman lafiya Sunakomawa gida akasoma shirye shirye"" kai Amarya su gwaggo hasana suka haushirya Khadija tuni labila tagama shirya kayanta""" anagama sallar magrib akafito da itah muktar dakinsa yashige yanata kuka kamar karamin yaro Hakan yakasa khadija tasoma kuka itama dakyar akafitarda itah gidan su inna masunkara datasu nasihar labila motarsu daya da khadija sukahau hanyar kaduna Sai wajajen karfe takwas sukakai duk da gudunda sukeyi harcikin mota banda kuka babu abunda khadija takeyi har akakai gidan maidagi yahangame masu kofar gidan motoci sukafara shiga gabadaya saida harabar tacika labila tayimasu jagorah hawa nahudu gabaya ansauya tsarin bangaren komai sabo hul akazuba gashi wajen yasha fentii sai kyalli yakeyi"" Amarya tashiga dakafar dama tareda addua Bayan tazauna sannan akataso gabadaya zuwa bangaren lubabatu balaifi tayi wanka tashirya Amman dazaran kacika kallonta zakasan tasha kuka tun nan labila Tasha jinin jikinta Dantunda sukashigo gidan tasan dadynta baibari akayi taroba sugwaggo hassana sukabata amanar Amarya Dan marainiyace takarba kuwa hannu biyu akaimasu nasiha daganan suka rankaya bangaren Amarya Akasoma kallon dukiyarda aka narkamata kai abun saiwanda yaganie"" Usman baishigo gidanba sai wajen goma hawanabiyu yatsaya Dan nan yamaida kayansa yarage kayan jikinsa yawatsa ruwa yayi sallah yanamai nuna godiyarsa ga Allah dabaiwarda yayimasa Ranar kwanan farinciki yayi washegari tundasafe lubabatu tasa akahadawa dangin Amarya abun karinsu saihada hadatake taware kamar ba itaba"" dangin khadija sunata yaba halayyar maman labila Anan sukaci abincin rana sannan sukasake gyarawa Amarya bangarenta dazasu wuce sukasake yimata nasiha tanakuka sukarabu labila takoma rarrashi haka akawatse hardare khadija batasakeba Suna zaune falonta bayan isha I"" Usman yaturo kofa yashigo da sallamarsa labila tagaidashi sannan tamike tabasu waje Falon kasa tasauka takunna kallo tana zaune lubabatu tasauko sosai tayi mama kin ganinta danbatasan sanda tazo gidanba kokuwa tareda Amarya tazo oho Labila tagaida itah ta amsa cikin sakin fuska tace yaushe kikazo??? Batareda takalletaba tace jiya aitare nazo dayan kawo Amarya Lubabatu tagyada kai batasake cewa komaiba tamiyarda hankalinta wajen kallon Usman ahankali yataka harsaman kujerah yazauna"" khadija gabanta yasoma dukan uku uku hannu yasaka yadago habarta saiyaga hawaye cikin muryansa maisanyi yace meyasaki kuka Deejarh na??? Kodai su inna ne dasuka tafi suka barki??? Kamar yace tasake fashewa dakukan yajawota jikinsa yasoma lallashinta haba Deejarh na kedaya kamata kiyi farinciki wannan baranar kukabace gidankifa kikazo karkimanta kinatareda annurin zuciyarki Kukanki zaisakani adamuwa Dan Allah kidaina yimun asarar hawayenkin nan masu matukar tsada"" shiru tayi saidai tanajan ajiyar zuciya sannu sannu saboda kukanda tayi"" yace kokefa idankuma kikasake yin kuka nima zantayaki kintaba ganin kukan babban mutum??? Dariya tasoma tasake shigewa jikinsa tana girgiza kai"" shima dariyar yayi yace toyau zakiganie inhar nasakejin kukanki nima zanbude bakina harmakota sujiyo Dariya takamayi tanaboye fuskarta cikin rigarsa murmushi yakeyi sosai yace kinci abinci kuwa??? Kai ta gyada yace banyardaba yanaji cikinki yadame??? Yayi maganar yanashafo Dan lafaffen cikinta Tace wlh naci dasahiba kuma banajin yunwa"" yace kintabbata tasake gyada kai yace shikenan kitashi kishirya saiki kwanta kihuta nasan haryanzu gajiyar biki bata fita jikinkiba zanturo labilar saiku kwanta tare hamdala tayi acikin ranta tace to Jayeta yayi daga jikinsa yadago dafuskarta yana kallo duk da tasaukarda kwayar idonta kasa cen kasan makoshi yace Deejarh Na kinyi matukar kyau jinakeyi kamar intasaki gaba inyita kallonki hargari yawaye. Bana gajiya dakallon kyakkyawar fuskarki Idanuwanta talumshe dukkansu wani yanayi suka samu Kansu aciki Usman karamin bakinta kawai yaketa kallo sosai danbakinta yana burgeshi Baisan sanda yamanna labbansa akan nataba""" sosai kirjin khadija yacigaba da bugawa Amman batayi kokarin hanashiba Yajima sosai yana sunbatarta ganin yakusa rasa natsuwarsa yanashirin wuce gona da iri Yabaiwa kansa hakuri saida ya tattaro sauran jarumtarsa sanann ya iyah raba kansa dajikinta mikewa yayi dasauri haryakai bakin kofa sanann yacemata saida safe dakyar muryansa takefita Khadija batace komaiba haryabar dakin tadade zaune awajen sanann tamike tawuce dakin tasoma rage kayan jikinta tawatsa ruwa tadauro alwala tana fitowa tasamu labila hartayi shirin kwanciya darduma tashinfida suka soma karatu Saiwajen daya saurah suka kwanta""" kowanne zuciyarsa fariii nikam nace banda mutum daya saida suka kwanta khadija tasoma tunanin abunda yafaru dazu wani nishadine taji yakamata filo tajawo takankame jitakeyi tamkar Usman ne aga banta bangaren Usman ma hakane danko abinci baiciba yadade yana tunani kafin barci yakwasheshi Washe gari anayin asalatu Usman saida yafara tashinsu sannan yawuce masallaci dayan aikin gidan tunda sukai sallah basu komaba sukasoma karatu da azkar din safe Saida haske yafito sukagyara dakin dakuma falon suka kunna turaren wuta nantake gidan yagameda kamshi"". Sukai wanka sukazauna sunafirah Usman yashigo dakin""" Labila tagaidashi ya amsa cikin sakin fuska yatambayeta yasuka kwana tace lafiya qalau fita tayi tasauka kasa tasamu har lubabatu tagama hadawa kowa abunda zaici gefedaya tazauna bayan tagaisheta Tacigaba dalatsa wayarta"" bayan fitar labila kusa da khadija yazauna tagaidashi ya amsa yacemata ya bakunta??? Tace babu hannuntà yariko yace tataso suci abinci bamusu tamike sukafito Tunda sukasauko taga mom din labila tayisaurin cirehannunta jikin nashi shima baiyi kokarin hanataba sunakaiwa harkasa taduka tace mom inakwana lubabatu ta amsa bayabo bafallasa Lafiya kalau Amarya yakwanan bakunta??? Tace alhamdulillah Usman yajamata kujerah yanuna mata tazauna sannan shima yazauna lubabatu tazauna gefe sunsakashi tsakiya kenan sai lokacin labila tataso tazauna kusa da khadija tature nata gefe tasoma cin dankalin dakecikin farantin khadija suka kalli juna tasakarmata murmushi tace bisimillah Usman baice komaiba sai lubabatu tace labila menene haka baganaki nanba yazakisaka mata hannu anata saikace warinki Labila hannunta ta tsantsame acikin plate din tana kallon Usman tace dad inaji kamar bakasanarda mom yanake da wannanba??? Tayi nuni da khadijar batajira mezaiceba tacigaba Tanamai kallonta mom wannan kawatace ko agida tare mukecin abinci anandinma tare zamuci inasonta fiye da kaina "" wlh koruwa banyarda sahibata tashaba saitaredani Idankuma ba za abari naci tareda itah ba to itama bazataciba saidai muje mugirka namu ta mike sahiba tashi muje"" khadija takalleta kamar zatayi kuka Sam bataji dadin abunda tayiba wannan yanuna tana zargin mamantane Usman ne yakalleta yace haba labila meyasa kikeyin haka??? Tace tomenayi dad daganafadi gaskiya nibana iyah cin komai saitareda itah Yace shikenan zauna kuci yakalli lubabatu wacce tasaki bakii hangaga tana kallonta yace kiyi hakuri kibarsu surikaci tare"" tasaki murmushi bakomai dadyn Abdul nibandamuba abunda yasama nayi magana naga kamar baidace taci abinci da matar ubantaba bansan kawarta bane Tunda hakan tafiso aishikenan nimeye nawà aciki Aisha✍🏼. [3/12, 7:32 AM] Adam yunus: [3/11, 7:51 PM] 1man: ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠ Chapter 81 By Gentle Lady💃🏽 Yasaki murmushi babu uwargida sarautar mata"" sosai taji dadin wannan sunan dansaida tadan dara har hakoranta suka bayyana "" labila bata koma kantaba tacigaba dacin abincinta Waifa abunda yasaka tayi hakan waikoda lubabatu tanada niyar sakawa khadija wani abun dole tafasa inhar batason abun yashafi yarta Illaikuwa kamar komai lubabatu take kitsawa azuciyarta tamkar suna shawarane tareda zuciyar labila dankuwa tayi alwashin dazaran khadija tasaki jiki dacin abincinta guba zatazuba mata taci idan tamutu saitasa *hatsabibin boka* yarufe bakin kowa tayanda babu Wanda zai tuhumeta tagama yanke wannan shawarar saigashi labila tawargaza Tagefen ido take watsamata harara tayanda itah kawai takeganie wacce akeyi dominta"" lubabatu tarasa wace irin yatahaifa wacce batason cigabanta itah tanayin komai saboda tasama masu gata Amman labila bataganie Anacewa idan kasabawa iyayenka zakahaifi kaima Wanda zaimaka fiyedasu itakam bataiwa mahaifiyarta katsalandar cikin al amurranta ko maganie tasamu mom dinta tasakawa dad bata fadamasa Dan abun baima dametaba Watarana ma agabanta sai mom dinta suyita firah da kawayenta yanda tamallake dadynsu Amman batajin komai kuma bata tabaji aranta zata tonawa mahaifiyarta asiriba Saigashi itah tahaifi yarda takenema tatona mata asiri wai anyama bamusayarta akamun danaje wajen scanning ba??? Dakamar wuya yarinya kamar haihuwar hafiza komai nata saitasaka Allah yace"" saiyanzu tagano dalilinda yasaka Usman yace yabarwa amayarsa sama kenan labilace tace bazata zauna nanba shegiyar yarinya dukta batamun shirina dole boka yakasa yinkomai lallai idan suna tare babu yanda zanyi inkasheta hmm baridai akwana biyu intuntubi *hatsabibin boka* hartacinye dankalinta bata fargaba saida tayita lalabar plate taji wayam"" bayan sun kammala tare suka mike zuwa bangaren khadija anan sukabar Usman sunashiga khadija tasha toka takoma gefe tazauna takauda kai daga wajen labila Dama labila tasan sai anyihakan kusa da itah tazauna tariko hannunta khadija tatureta kinga malama kirabu danie Murmushi labila tayi tarike kunnenta tace tuba nake small mom""" khadija tasoyin dariya Amman takanne tace banason wasa yanzu balokacin wasabane Labila saudari inasanardake muhimmancin uwa Amman bakyaji ahakan kikeso inzauna gidanku??? Gaskiya idan bazaki dainaba wlh zamubata dake kibarni narikacin abincina nikadai mana ko anfadamaki wani abunne zaisameni idaan naci nidaya??? Baidace kinazargin mahaifiyar kiba kizama mai kyakkyawar fahimta gakowa saikiga hakan yazama alkhairi agareki Labila hawaye tasoma sharewa tanason khadija kodon fadamata gaskiya datakeyi subasusan komaiba itakanta tanason mamanta Tanaso tazama uwa tagari tuntana karama datafahimci halin uwarta takeyimata nasiha Amman kamar cewatakeyi tacigaba Tundatake bata tabaganin mom dinta tadorah goshi akasaba dasunan sallah ashedai shiriya wata rahamace da Allah kesanyawa azukatan bayinsa Yashiryarda Wanda yaso kuma lokacinda yagadama"" yafitarda matacce cikin rayayye yakuma fitarda rayayye acikin matacce samun kanka dakayi acikin shiriya ba dubarar kabace bakada wata dubara Tamatso hawayenta Allah kaganarda màhaifiyàà gaskiya "" kukanta yasaka jikin khadija yayisanyi tajikamar itace silar kukan nata Ta sassautodà murya tàce sahiba maganganuna sunkona maki raine??? Kiyihakuri bàdasoñ zuciya nafadi hakanba Nafadane saboda inajin tsoron gobe kiyama atuhumeki akan rashin kyautatawa mahaifiyarki dabakyayi komai lalacewar mahaifiya mahaifiyarkice Kodakuwa kinga tanayin abunda baidaceba saikiyita yimata nasiha kinayi kinayi sannu kan hankali saitagane gaskiya kinga kinsamu lada kuma kin kyautatawa mahaifiyarki "" ballantana babu abunda mahaifiyarki takeyi namuni wlh naji ta sake shiga raina hakurinta dasanin yakamarta kallifa yanda ta tarbi yan uwana hannu bibbiyu yanzu irin wannan matar kikabari akayomata kishiya??? Saiyanzu nake zargin kaina anya banshigo huruminda banawaba??? Banaso nayi sanadin shiga tsakanin masoya irin haka sukadai sukasan irin sonda sukewa junansu meyasa tunfarko bakisanarda niba sahiba Labila takalleta da mamaki ganin itama kukan tasoma tace wlh indai akan mamana kike zubarda hawayenki kimadaina karkiyi hasararsu Kuma naji nasiharki zankiyaye Amman kisani nangaba dakanki zakigano abunda ninake hangowa kumani bazarginta nakeyiba yazan yi inzargi uwata kawaidai saboda nasabacin abinci dakene haka zalika wlh banajin dadin abinci indai nidaya nakeci Cin abinci cikin taro yafi dadi gakuma kara dankon zumunta dakuma soyayya ko agidan hajiya kinaganie indai nikadai zanci abinci tokuwa bazanci komaiba Amman idan kinga zantakura maki agidan mijinki kiyi hakuri zuwa gobe zandauki kayana inkoma kano inbarki da masoyanki kiyi hakuri dabata maki raidanayi tamike tsaye dasauri khadija tajawota tarungumeta tanakuka yazakice haka sahiba wlh bazan iyah zamaba idan bana ganinki Dan Allah kidaina cewa zakitafi dagayau bazansake yimaki maganaba komai kikace nafahinceki yanzu Amman kiyi hakuri kinji"" jayeta tayi ajikinta tace tonidai kukan ya isah kar daddy yaga idonki yayi ja yadauka dukanki nayie Khadija cikin kukan tasoma dariya""" tace kaisahiba dukadai kamar jaririya""" tarausayarda kai ato nasan yanda dad yakesonki dazaran yaga idonki yayi jajir bama zainemi ba asiba zaihauni da duka khadija tace kai sahiba da abun dariya kike wlh Hamma tayi tace nifa barci nakejin zandan kwanta inhuta"" labila taharareta tace nikuma dabanajin barcin intsaya gadinki koyaya"" Khadija tarike kugu tace kohakan kikayi aibaki fadiba tunda nikikayiwa"labila tace hakafa Amman bazanyibaa dannima barcin nakeji Amman bari nasaka kaset danazo dashi insaurara harbarci yasureni tayi maganar tanabude Jakarta faifan CD tadauko takunna DVD tasaka Kaset din aka soma da bisimillah complete Qur"an ne tundaga bakara. Har nasi kira ar sudes gabadaya saman kujerun falon suka kwanta sunkashe kunne suna saurare harbarci yasuresu lubabatu datake bangarenta tuni tasoma jintashin karatun tamkarma abangarenta akeyin karatun Aranta tace waime wadan nan mutanen suke nufi??? Zasumiyarmun dagida makarantar islamiyya ko masallaci to wlh dasake yanzu ana wannan karatun yama za ayi ta iyah kiran *hatsabibin boka* taja tsaki ninasan duk iskancin labilane""" tashi tayi tasauko kasa danyafi Dan dama dama bakajin karatun sosai Su labila tuni barci yayi awon gaba dasu sai biyu saurah suka farka sukasakeyin wanka sukai alwala suka gabatarda sallah"" bayan sunshirya suka sauka kasa"" daidai shigowar Usman gidan yakurawa Khadija ido danba karamin kyau tayiba yadine ajikinta irin mai rawar nan anyimasa doguwar Riga sama yadan matse kasakuma saiyabude takama gashinta duka baya tanannadeshi da dankwali tayanda ko silin gashinta ba aganie kodaya""" Bawata kwalliya tayi sosaiba manbaki kawaine tasaka sai powder Amman tayi kyau fuskarta tafito tayi haske"" kallonda yake jifanta dashi tuni taji ajikinta bayan sun zauna tadago ahankali tayimasa sannu dazuwa ya amsa labila ma taimasa ya amsa yamasu yazaman gidan sukace Alhamdulillah Yawuce hawa nabiyu kamar yace khadija tabishi Amman bazai iyah ba bayan yawuce labila tahau zungurarta harsaida yahaye tace waike haka su gwaggo suka koyamaki mijinki yadawo yakwaso gajiya ananma zakiyimasa sannu dazuwa??? Wlh koki gyara ko in tattara inbar maki gidan"" talangwashe kai toyazanyi sahiba???/ au bakimasan mezakiyiba tashi zakiyi kije kihadamasa ruwan wanka idan baicire kayaba kitayashi ke inhar takama kiyimasa wankan saikiyimasa menene bamijinki bane aituni khadija tarufe fuska tace wlh baxan iyah ba sahiba Labila tace tosaiki zauna tajuyamata baya"" Khadija tayi shiru ganin labila taki ko kallonta yasaka tatashi tace tonatafi tawaigo taballamata harara tace kimaxauna tamurguda mata baki khadija tagirgiza kai kawai tawuce zuwa saman kamar kazarda kwai yafashewa aciki Kofar dakin tayi tsaye tana tunanin shiga daga karshe kawai tayanke shawarar shiga. Idonta arufe waikarta sameshi yacire kayansa da sallama tashiga shikam abumma saiyaso bashi dariya yana kwance saman kujerah dakayan jikinsa danyana shiga yazube akan kujerar ya amsa mata sallamarta saikuma tayi tsaye kallonta yakeyi tundaga sama harkasa yalumshe idonsa ahankali yace kikaraso mana!! Dakaji muryarsa kasan dakyar yatattaro haruffan yayimata magana Aisha✍🏼 [3/11, 7:52 PM] 1man: ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠ Chapter 82 By Gentle Lady💃🏽 Ahankali tatako inda yake Amman bata zaunaba hannunta yajawo yayi mata mazauni akan cinyarsa kanta yanakasa tana wasa dayatsunta Yadago fuskarta ahankali yace Deejarh na meyasa bakason kallona ne kodai fuskata tsoro take baki??? Kara sanne kanta tayi tana girgiza kai yace nibanji mekika ceba magana zakiyi"" ahankali tace ah ah"" yace inhakane saiki dago ki kalleni Ahankali tadago takalleshi idanuwansu suka sarke Dana juna kowanne zuciyarsa bugawa takeyi kamar ganga""" dasauri khadija tasanne kanta bata iyah jimirin kallon cikin idonsa yanayimata kwarjini sosai sake dago fuskarta yayi wannan karon idanuwanta alumshe suke hakan yabawa Usman damar sunbatar labbanta Yadaukesu tsayin mintuna ashirin yana wasa da itah ko bihim bataceba kuma batayi yunkurin hanashiba dankansa yagaji yasaketa yajingina kansa saman kujerar yana maida numfashi""" Haryanzu tana nan indatake sai saukarda ajiyar zuciya take ahankali"" yadade kwance saidayaji yasamu natsuwa sannan yadago akasakalance yace kinci abinci kuwa??? Kaitagirgiza alamar ah ah Yace to tashi kihadamun ruwan nayi wanka kobashi kikazo tayaniba"" batace komaiba tamike zuwa toilet din tayi addua sannan tashiga tahadamashi"" ruwan tanacikin toilet din bata fitoba harya gama cire kayansa"" yasameta toilet din Yace waiharkin hada shine bakizo kinfadamunba kika tsaya anan kodai wankan zaki tayanie??? Cikin zolaya yayi maganar Aikuwa zumut tafito tace ah ah ba amfanie a aje ruwane abayan gida afita saboda shaidanun aljanu sunayin wanka aciki kaikuma idan kashigo bakaganin sauyin komai saikayi wanka dasu hakan yanajawo safuwar jinnu dakuma cututtuka da shaidanun aljanu kan iyah jefar mutum dasu Kaiyagyada alamar yagamsu """ yashiga ciki tareda addua yarufe ko far wajenda yake ajiye kaya tabude tarasa kalar kayanda zata daukar masa shiru tayi tana nazari Wadansu kananun kaya taciromasa jar rigace da bakin wando "" rigar tanada dogon hannu tayita juya kayan waikomadai bayason kananun kaya??? Farar singlet tadora masa Saikuma ta aje tafesamasu tirare wayarsa tadauko tashiga massage tayi rubutu ta aje saman kayan tafita falon tazauna jiransa Bayan yafito wanka baisameta dakinba yaga kayanda taciromasa wayarsa dayagani da haske yadauka Bansan irin kayanda kakesoba nafitomaka dawan nan idan basuyiba saika sauya"" murmushi yayi ya aje wayar yashirya yasaka kayan rabonsa dayasaka kananun kaya haryamanta"" yataje sumarsa yagyara dankaramin sajensa saiyafito a Usman dinsa Murmushi yayi lokacinda yakalli madubi yagirgiza kai wayarsa yadauka yasaka agefen aljihunsa nawando yasa daya abaya sannan yafito Tunda taji kamshin turarensa tadago kanta tadauka baisaka kayanba saitaganshi sanye cikin kayan yayi masifar kyau tayanda khadija takasa boye kunyarta takuramasa ido cen kasan makoshi tace masha Allah tsarki yatabbata ga ubangijinda yahalitta wannan surar"" tsaye Usman yayi agabanta yasaka hannunsa daya acikin aljihunsa yana sakarmata murmushi Jinkamshinsa"" gab da itah yasaka tadawo daga duniyar tunaninda taje""yace Deejarh na nayimaki kyaune??? tagyada kai saiyanzu tadanji kunya murmushi yayi yashafi gefen fuskarta yace muje muci abinci yunwa nakeji batace komaiba suka jerah zuwa kasa Lubabatu da labila suna zaune saman dinner sukawai sukejirah kusan tare suka kallesu yanda sukajero sunyi kyau Sundace dajuna Usman yadawo kamar danshekara ashirin dabiyar Wani mugun kishi lubabatu taji waidama haka Usman yakeda kyau??bata taba ganin shigarda taburgetaba irin wannan Harsuka karaso batasan sun kawoba saida khadija tace mata inayini"" tace uyum lafiya qalau Amarya anyinie lafiya qalau tace sannan suka zauna lubabatu tazuba wakowa saita hadewa labila da khadija sukasoma cin abincin labila kam dadi kamar yakasheta kobakomai tasan yanzu dadyn ta yasamu matarda yadade yana nema kuma insha Allah babu abunda zaisamu sahiba"" wajen yayi shiru bakajin motsin komai sai karar cokullah kowa da abunda yake sakawa aransa"" bayan sun kammala"" Usman yamike yana kallon agogon hannunsa yakalli lubabatu yace yau Abdul zaikoma tundazu inataredashi yanzun ma nadawone inyi wanka saboda zafie Tace habadai harzasu koma bazasu jirah suyimana ko sati dayaba??? Yace kinsan akwai aiki sosai idan zaiwuce zaikawo madam kugaisa nizanje kano yanzu"" tace to Allah yakiyaye yakalli khadija yace kina bukatar wani abun??? Kaita girgiza alamar ah ah yace shikenan sainadawo tace adawo lafiya Allah yakiyaye yace Ameen sannan yawuce Labila tahau zungurarta tana nokewa saboda lubabatu tana wajen abun yabawa labila haushi ta mike taja hannunta saida takai bakin kofar tace saiki wuce khadija takalleta saitaga tana harararta tasakai tafita itakuma tajuya takoma cikin falon tazauna tana kallon wayarta kamar batayi komaiba Lubabatu kuwa binta kawai takeyi dakallon mamaki watoma itah yarinyar tanada kunya dakuma kawaici yartane batasanshiba lallai dole taraba tsakaninsu wanann shegiyar abotar dole abarta"" 🙄 Usman yana bude mota zaishiga yahangota tajikin glass murmushi yasaki danyasan aikin labilane Dan indai Dan khadija yanda takeda kunya bazata iyah tasowa agaban lubabatu ba Tanakawo wa wajen yasoma dariyarta ganin ta shake kamar zatayi kuka yanzu idan takoma dawanne ido zata kalli mom itah gata marar kunya hardawani zuwa rakiyar mijie Yace menene Deejarh na??? Tace bakomai motar yabude yace tashigo ciki babu musu tashiga yace naga kamar ranki abace kokinazuwa inje dake??? Murmushi tayi tace sokakeyi Yayana yadakeni??? Yace akan mezaidakeki bayankuma kinataredani Tace tabdi wlh bakasan halinshiba aizaice yaushe aka kawonie harnafara yawo idan kaje kakarbomun wayana wajen inna namanta bandaukotaba"" yace shikenan yasunbaceta akumatu yace sainadawo tace adawo lafiya tafita tarufemasa motar tana tsaye saida taga wucewarsa tajuya tàkoma fàlon kanta yanakasa tashiga da sallama Labila ce ta amsa cikin jindadi kusa da itah tazauna idonta haryanzu yana kasa abunyabawa labila dariya tahau yimata dariya saida taga alamar zatayi kuka sannan tadaina tace sorry small mom bazansakeba ayimun murmushi mana Khadija takaimata duka tagoce sukahau dariya lubabatu tanagefe tana kallonsu mikewa tayi tace labila kizo inason ganinki tawuce zuwa sama Labila takalleta takalli Khadija batace komaiba harkusan tsayin min tuna goma da tafiyarta sannan khadija tace waiba kiranki mom tayiba naga bakida niyar tashi Tanisa sannan ta mike tace tashi muje"" harararta tayi tace bangane intaso mujeba kikasan kiranda mahaifiyarki takemaki kijemana kinsan akwai sirri tsakanin uwa daya"" Labila tace tonidai idan bazakiba nima zamana zanyi"" khadija tace au ashefa badadi tokizauna Amman wlh nima duk kikasake cewa inje wajen daddy idanhar batare zamujeba nima bazaniba tamurguda mata bakie Labila tawaro ido tasan khadija zata aikata hakan tace rufamun asiri nidanakeso asamamun Kanwa barito naje nidai tawuce tana dariya""" khadija tace Allah yashiryaki sahiba Da sallama tashiga ban garen lubabatu tana saman kujerah ta amsa sallamar kasa tazauna tacemata ganie lubabatu tayi murmushi tace saiyanzu saiyanzu uwartaki tabaki izinin zuwa tundazufa nakiraki Kanta yanakasa tace karki daukarwa kanki wani hakkin wandama yake kanki ya isheki ni sahiba batahanani zuwaba hasalima banyi niyar zuwaba itah tasakani dole Danbakyau kisamu mutum biyu sunafirah batareda kinnemi izinin ganin dayanba kijadaya agefe wani abuñ zaitaba zuciyarsa Haryayi tunanin kodai maganarsa za ayi lubabatu tamere baki tace wannan kuma kutashafa tayi shiru nayan dakiku sannan tace labila inaso kifadamun mewannan yarinyar tafini dashi dakike sonta nibakya sona karfa kimanta Nice nahaifeki duk wani Wanda zakiso yasoki bayana yake Labila tayi murmushi tace kwarai mom nasanda haka nima inasonki irin sonda ya takeyiwa nahaifiyarta halayenkine banaso saboda sun kasance ababen kyama Kinsan makomar Wanda yakashe musulmi kuwa??? Bayankuma alhakin daddy dakike dauka idan harxaki watsarda miyagun halayyarki wlh zanbaki mamaki danzandawo tamkar kare agaban sugabanta Lubabatu tamurmusa tace ke yarinya ce labila haryanzu kuruciya tana cinki nifa gatane nakeyimaku amatsayina Na mahaifiyarku banaso kobayan ran mahaifinku Ku tagayyara Labila takalleta da mamaki tace kekintaba tunanin mutuwarki??? Gaban lubabatu yabada rasss hartaruntse idonta Kokintaba tunanin wannan dukiyarda dady yatara bazata kareba??? Ai ahaifi da da arzikinsa yafi amutu abarmasa gado duniyar nan dakike ganie bafa matabbata bace koshi bokan naki yafadamaki shibazai mutuba wlh boka makaryacine mom yanaso yabatardakene dake dashi idan har kuka mutu Baku tubaba wutace makomarku kiwatsarda duka abunda yabaki kidogara ga Allah shine zaibaki duk abunda kikeso Afusace lubabatu tamike tayanka mata mari tace rufemun baki shashasha wacce batasan maisontaba tunkafin. Ahaifeki nakejin irin wannan wa azin ga malamanda suka keceki awajen karatu Amman kokadan baiyi aiki akainaba sai wanann maganar taki kedabanda bokana harma za ahaifeki kekanki darajarsa kikeci wlh Labila tadago cikin kuka tace wlh karyane nibabu wani kazami mushiriki daya isah inci darajarsa shaidan kawai inna kintata daidai dadyna bama cikin hayyacinsa ya aurekiba kaico ni labila meyasa mahaifiyata tazama haka daga ina matsalar take??? Lubabatu tace tashi kibacemun daganie kuma nasan duk take takenki wato ke gamai Kawa?? Nibabu ruwana da kawancenku idankuma baki fita sabgataba harke zansa agama dake dannalurah kinashigarmun hanci nagaji da abunda kikeyi kinsoma shiga huruminda banakiba Labila tasaki murmushin takaici tace kisa yakasheni mom saimuga idan agurinshi rayuwata take nikoda mutuwa nayi wlh banda takaici me akeyi dawannan kazamar duniyar maitattareda da dauda da kazantar masu halayya irin taku dake da bokan naku sainaganie idan kudin zaku gujewa mutuwa "" ta mike hartakai bakin kofa tace kiyi hakuri mom banason muryana tana zarta taki awajen magana kigafarceni Allah yaganardake gaskiya tabude ko far tafita anan tabar lubcy tsaye rayuwarta intayi dubu tabaciii kirjinta kamar zai balle kofar dakin takulle tawuce kuryar dasauri danfa dole *hatsabibin boka* yasan matakinda zaidauka akanta Aisha✍🏼 [3/11, 7:52 PM] 1man: ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠ chapter 83 By Gentle Lady💃🏽 Dasauri takarasa wajenda ta ajiye akwatin madubinta tadauko tafito dashi tashafa tareda kiran sunan *hatsabibin boka* saigashi haske yayi tartsi saigashi ya bayyana saman kujerarsa idanuwa jajir lubabatu tasoma magana Haba boka waimeyasa hakan Ashe akwai lokacinda zanga irin wannan ranar yata tacikina tana nema tafi karfina??? *hatsabibin boka* yakece dawata mahaukaciyar dariya yace babu abunda banganiba acikin madubin tsafie na kisani wannan aikin bakaramin aikibane dole kirabasu indai kinaso kiga karshen wannan yarinyar Cikin damuwa tace yazanyi inrabasu boka??? Kaima kasan labila idan tanason mutum bazata taba barinsaba dama batasan shirina akantaba dasauki Amman yanzun bazata taba yarda inrabasuba Yasake kecewa da dariya yace cikin sauki zakirabasu tace taya kenan boka??? Yamurmusa kicewa mijinki yakamata suje yawon shakatawa kodan sumore amarcinsu tunda kinlurah Amarya kunya takeji bazata sake jikinta ananba Lubabatu taware ido tace habadai idan nayihaka anya banyi wautaba??? Wata razanannar tsawa yadakamata yace nifa ba amusu danie dazaran nace ayi kaza kar atsaya yimun musu idankuma bahakaba narantse dagirman tsafina bazanji tausayinkiba wajen nunamaki kuskurenki Tuni jikin lubabatu yahau kyarma kamar mazariii tadukadda kanta tubanake yakai wannan gawurtaccen boka man tawa nayi Amman zankiyaye gaba Batareda ya sauraretaba yace idan kin aikata bayan suntafi saiki nemenie yabace battt yaufa lubabatu tabatawa boka raiii jitake gabadaya duniyar tayi mata zafie kamar wutaa jin Kamar ana kwada sallama yasaka tamiyarda komai tashiga toilet tawanko fuskarta tadan goga powder tafesa turare sannan tabude kofa tafita matar Abdul ce tana ganinta tasaki fara a tace karaso mana Hauwa u"" koda yake nayi fushi tunsanda kikazo sunan Abdul bakisake zuwaba karasawa tayi cikin falon tazauna tana dariya tace haba Anty luba kinsan balaifina bane wlh tunsanda mukaje minna bansake dawowa nan ba dadyn ameer ne kawai yake zuwa koshi bayawuce kwana daya kema kinsan danazo aidole inzo nandin saboda ke Lubcy tace hakane ina yaranki ainasan yanzu kinyi haihuwa biyar ko??? Hauwau tarike baki tace lala Anty luba kebakiyi biyarba saini kanwarki"" lubabatu tayi dariya tace aimu munbarmaku bakiga Dan autana yagirmaba Hauwa u tace inazanganshi labila kawai naganie ai"" nima haihuwana uku biyu mata daya namiji Asiya kausar sai Muhammad inakiranshi ameer dansunan babane"" lubabatu tace masha Allah Allah yarayamana su tace Ameen bari nasa akawomaki ruwa""" Ah ah dakinbarsu labila tabani ruwa wlh tundazufa mukazo su asiyama sunakasa nabarsu"" tace shikenan ya minnar??? Tanacire mayafinta tace Alhamdulillah ai inasaran kwanan nan zandawo garin nan nagaji dazaman cen bansan kowaba saidai makota ko anawani Abu saidai kaji labari nacemasa yayi aure kawai saiyaje da amaryarsa nikuma inzauna dani da Yayana Kallon wata marar wayo lubcy taimata tace lallai Hauwa wasu suna gudun kishiya kekuma harnemanta kikeyi??? Tace to menene Anty luba arzikinefa ai abun farincikin kine mijinki yakara aure alamun kunada wadatar zuci kenan ni wlh koda hudu zaiyi inaso kowafa da halinta zata zauna nasandai duk inda zaije yazagayo kaina zaidawo dannice uwargida kingakuwa girmana bazai taba faduwaba kobayan raina za adinga yabamun insamu kyakkyawan shaidu aduniya yafi inmutu inbarwa Yayana abun fada Tuni lubcy tadauke wuta kardai hauwau tasan abunda nake aikatawa??? Takatse mata tunani dacewa amaryarki taburgeni wlh gata karamar yarinya zakuji dadin zama dajunanku dannalurah saitayi hakuri Lubabatu tace hakane kam wlh ai inata addua dadyn labila yayi dace kinsan matan yanzu sai ahankali watama kina zamanki lafiya damijinki dazaran tashigo saitatashi rabaki dashi Matanda yake aurah duka banakwarai bane Amman wannan kam ina tunanin andace!" Hauwau tace hakane dadyn ameer yasanardani ai Allah yasake shiga tsakaninmu da mugayen mutane lubcy tace Ameen Mikewa Hauwa tayi lubcy tace waiharzakiyi me??? Tana yafa mayafinta tace tafita mana kinsanfa jirgi bazai jiramuba dole mujirashi dalokacin tashinsa yayi zaitashi tace hakane tamike turarukka dakayan shafawa tahado mata suka sauko kasan sun samesu sunata firah kamar dama sunsaba dajunansu duk Asiya tace kunga har mom tafito tonidai Anty kibamu number muyi chat Labila tace wlh bata chat saidai kuyi waya kuma banama tunanin tazoda wayar inaji tamantata agida saidai inbaki tawa Tace shikenan suka karbi number labila lokacin har su lubcy sun kawo wajensu tare sukai masu rakiya harkofa saida sukaga tashin motarsu sannan sukadawo Daki suka wuce kaitsaye danyin sallar la asar bayan sungama sukai zamansu adakin"" lubabatu Sam takasa jinta daidai tun abunda tayi yazama dole tasake kiran boka tabashi hakuri hakan kuwa akayi tasake kiransa tabashi hakuri yace ya yafemata Amman kartasake aikata irin wannan kuskuren tace tagode zatakiyaye Yace nasan abunda kike tsoro kisani babu abunda zaishiga tsakaninsu duk abunda yakefaruwa dasauran matansa itama aikin yashafeta muddin yayi niyar hada shinfida da itah zaisamukansa yana kyamarta saboda warinda zatarikayi kamar mushe Dazaran sunbar kasarnan zakiga laya a inda nasaba aikowa a ajiye maki kije kisamu wajenda kikasan kullum sai anyi dahuwar abinci tundaga safe hardare"" saiki tona murhun kisaka layar karkibari kowa yaganki dazaran kinyi haka kingama komai Yanda kikasan zafin wuta idan kikaje kusa da itah haka jikinsu zaiyi zafiii dazaran sun kusanci junansu zasuji kamar zasukama dawutaa dole su nisanci juna tahakan hankalinta zaitashi tadaina samun lokacinda zatazauna tayi addua saboda tunani alokacinne zamucika aikinmu akanta. Wayyo dadi tuni dadi yalullube lubcy tahauyimasa godiya yace maganar labila tabarkomai ahannunsa shiyasan yanda zaiyiii Tayi masa godiya tace zaiga sako aranar ta siye dabbobin ta aikamasa"" cikin kwana biyu tasamarmasu biza dakomai dantasan inhar cewa tai sutafi labila tana iyah cewa saitabisu wannan dalilin yasaka taiwa tufkar hanciii Aisha✍🏼 [3/12, 9:24 AM] 1man: ☠ *HATSABIBIN BOKA!!!*☠ Chapter 84 By Gentle Lady💃🏽 Zaune suke dadare suna cin abinci lubabatu tace nikuwa yau akwai maganarda nakeso muyi dakai""" yakalleta yace Allah yasadai lafiya ??? Tarausayarda kai tana kallon khadija cikin fara a tace insha Allah baridai mukarasa cin abincin"" yace nidai kifadamun yanzu kinsanni da zumudi kamar sabon angwo gabadaya suka kwashe da dariya harsu labila"" Yace tokokunga laifina ninafison idan za afadamun Abu kawai afada yanzu kafin mugama bakisan iyah jaye jayenda zuciyata zatayiba""" adaure afadamun Cikin siririyar muryanta tace daddy kasanfa ba amfanie ana cin abinci ana magana kamar bakabawa abincin mahimmanciba""" yakalleta gaskiyarkifa Deejarh tobari mugama yayi maganar yana kallon lubabatu murmushi kawai tayi tacigaba dacin abincinta Aranta tace wannan hartasoma tafi labila iyah yi shi abincin harsai anyiwani girmamasa 🙄"" tsaki tayi aranta tacigaba dacin abincinta"" bayan sungama sannan yakalleta yace karfa kice naciga zanzari nasan duk abunda zaifito bakin nan naki alkhairine murmushi tasaki har hakoranta suka fito tace ko??? Yace koma zakice ainidanake dake nasan haliinki fiye dake kanki""" labila kam murmushi tayi aranta tace kadaisan Wanda kasani amman babu Wanda yasan halin mom sai Allah nda yahalicceta""" Tace hakane abunda yake gefenta tadauko Tamika masa tana murmushi shima murmushin yakeyi taredakuma mamakin menene aciki??? Tagane abunda yakenufi tace kabuda kaganie mana""" bamusu yabude biza ce tazuwa Dubai Baki sake yake kallonta yace biza naganie??? Tamurmusa ah takuce "" tanisa tana kallon khadija tace wannan itace kyautar taya murnar auren Ku nabarku kumore amarcinku har Kanwata tasamu rabo""" dasauri khadija tasun kuyarda kanta kasa saboda kunya Usman yarasama dawadanne irin haruffa zaiyi amfani domin yagodemata dakyar ya iyah hadiye yawun bakinsa dasuka kafe yatttaro sauran maganarda ke bakinsa yace Maman Abdul wai dagaske kike kuwa??? Tagyada kanta sosaima aikasan inason farincikinka fiye da nawa inaso kasamu cikar burinkane bazanso kacigaba tatauyewa kanka hakkiba Nalurah kanwar tawa bazata saki jiki dakaiba saboda tanada kunya shiyasa nashirya maku tafiyar kozatadan sake dakai Yasaki lallausan murmushi Alhamdulillah amman naji dadi sosai bansan dawadanne irin kalamai zanyi amfanie wajen godemakina tnx matata Murmushi tasaki najindadi tace basaika godemunba wannan aikinane nashirya maka kayanka""" sauran nata tashirya dan jirgin shadaya zakubi Yayi murmushi yana kallon khadija takasan ido wacce haryanzu idanuwanta suna kasa kosaudaya bata dagoba"" labila kam tashiga tashin hankali dankuwa tana tunanin wannan abun kamar wata munakisar lubabatu tashirya Amman babu yanda zatayi tawargaza tafiyar tunda batada bakin fadin komai akan mahaifiyarta Amman alal hakika ranta baikwanta da wannan tafiyarba Dolene tasamu malaminsu saboda ayiwa khadija saukar qur Anie murmushi tayi afili sanin tasamo mafita lubabatu tana jefar labila da murmushi itama haka kowannensu shikadai yasan ma anar murmushin nasa Labila tace sahiba tashi muje intayaki hada kayanki dankinsan dasafe bazaki samu damar hadawaba tayi maganar tanajan hannunta Tamike jiki bakwari tabi labila kamar rakumie da akala sukuma suka rakasu da idanuwa lubabatu tanayiwa Khadija kallon kingama yawo yarinya tunda kika auri mijina Usman kuwa yanayimata kallon soda kauna yanarayawa aransa zaihuta sosai da Deejarh nsa" saida suka bacewa ganinsu sannan Usman yamike yaja hannun lubabatu suka dawo falon saman kujera suka zube Yakuramata ido yana murmushi itama shitakeyi tace yadai mijina""" yamuskuta lubcy wlh mamaki kikebani sosai"" tarausayarda kai tace mamakin menene??? Yace yanda kike kyautatamun wai anyama zamanin nan za asamu mata masu irin halayyarki??? Gaskiya baza asamuba""" tace nidai kadaina fasamun kai da dadin bakin nan naka Yajawota jikinsa yace badadin bakibane wlh dagaske nake nikam nayi sa ar mata tagari wacce kowanne namiji zaiyi mafarkin mallakar irinta""" Hawayene suka sauko akan kumatun lubcy sanyinsu yaji ajikinsa yajuwoda itah dasauri yace lafiya lubcy menene kuma nakuka??? Please banason kukan nan nakie Dan Allah kidaina Tashare hawayenta tace inajin takaiicin kaina daya kasance bana baka hakkinka dayake kaina yanda yakamata inayin hakanne kodan Allah yayafemun hakkinka danaketauyewa ninasan ina cutarda rayuwarka Banason inzama daya dagacikin matanda Allah zaiyi fushidasu Usman yadorah yatsanshi akan labbanta yace bakyacikinsu matata nibaki tauyemun hakkinaba aihakan Allah ya halicceki kuma kinayin iya kokarinki wajen ganin nasamu kwanciyar hankali nagode maki Allah yabarmu tare yasake janta jikinsa yana aikamata wani sako mai rikitarwa Al amarinsu labila kuwa suna hawa bangaren khadija tasheka dagudu saman gado taboye fuskarta""" labila mezatayi inba dariyaba saida tayi mai isarta tace wlh nifa mamaki kikeban kowaya fadamaki yanzun anajin kunyar soyewa danamiji Kinganni nan wlh idan nai aure saina baki mamaki Dan wlh agaban kowayema zannunawa mijina soyayya gashidai kin girmeni Amman ninafiki sanin yanda ake tarairayar miji Tazauna kusa da itah sahiba wannan tafiyarda zakuyi wata damace agareki daxaki saye zuciyar mijinki ki ajiye kunyar nan taki kinunawa mijinki tamkar dagake saishi kuke acikin duniyarku Idan kinataredashi kimanta dakowa kigamsarda mijinki Dari bisa Dari kedin tashice kuma mallakarsa tarage murya kuma wlh karyanemi kibashi hakkinsa kiyita gudunsa Khadija tamike takaimata duka tace waike yaushe kikazama marar kunya bansaniba??? Labila tace ke yarinya zauna nan ainadade inacemaki kifara chating kozaki koyi yanda ake ririta miji kinki hmmm wlh jinake damanice ke danatsula tsiya sai nasakawa wata hawanjinie😕😂 Khadija tatureta tace Allah yashiryaki mom din??? Tace au sorry namanta ashefa mom ce baridai inhadamaki kayan dannasan halinki innabiye maki manyan kaya zakidauka duka tayi maganar tana mikewa tabude drawer tajawo akwatin kayan khadija Tahau duba kayan ciki kananun kaya tayita shiryawa khadija saboda Usman yasiyamata kananun kaya masu masifar kyau Mini sket da kananun kaya gasunan kamar kazanta""" manyan kaya kala uku kawai tasakamata"" takoma hadamata kayan kwalliya komai saida tasaka tace sauran kuma idan kinje karkiyi kwalliyar""" nasan halinki"" danzankirah inji waima ina wayarki??? Khadija tace nafadawa dad fa yakarbomun gida namanta ta wlh kuma inason yin magana da Yayana Amman nakasa tambayarsa koya karbo kumashi baicemun komaiba"" labila tace kinsone wlh dakinason wayadashi aidasaikice inbaki Aron wayata saiki kirashi"" Tamere baki inna hardace nomber din kokuma inbar hardaceba"" labila tace kumafa hakane Amman aidason ranki lanbarda batawuce ashirinba keda kikeda kwakwalwa maikyau kikasa hardacewa Tace kwakwalwata ta karatuce bawai danna hardace tarkacen numbers ba""" labila tace hakanefa ustaziyya Amman kinsan hardace number yanada amfani kodan watarana Bawai ina fataba kisamu kanki inda kike neman agaji abaki Aron waya baki hardace number kowaba yakenan gashima dai yanzu karamin misali kinason waya da ya muktar Amman bakisan number saba Khadija tace kinada gaskiya zanyi kokarin hardace tamutum biyu"" labila tace Yayana dakuma daddy ko ??? Murmushi khadija tayi labila tace bakomai mukoda ba a hardace tamuba badamuwa Amman inafatardai abunda nafadamaki dazun kinkwasheshi afaifan kanki wlh sahiba inajimaki tsoron wata baturiya takwace makishi Aikuwa khadija tahade rai labila tahauyi mata dariya tatashi tabita sukahau zagayen dakin karshedai labila tafada saman gado tana hakiii tace tubanake small momy🤗 Khadija tace aisaikinsha rankashi aka"" labila tarumtse ido takankance kai tanadafe dakai tanajiran saukar rankwashi khadija tahauyi mata dariya tazube saman gadon tace waike atunaninki rankwashinki zanyi aka??? Ainibazan rankwashi kainaba idan dady yasamu baturiya aibanice zanyi kishiba kece dannasan kinfison farincikine fiyedani Kaina yanda kika damu dani nibandamu dakaina hakanba """ Labila tace aisaboda kinsan hakan shiyasa kikemun abunda kikaga dama takwanto saman kafafuwan khadija tace wlh sahiba jinakeyi kamar aduniya bazanso kowa sama dakeba Idan akacire Allah da manzonsa da sahabai dakuma ahalal baitiii idan za akuma tambayana wanakeso bayansu kinsan wazanfada??? Khadija tagirgiza kai labila tace wlh sahiba sunanki zankirah !! Jinake tamkar sabodake akayini kullum soyayayrki sake shiga rainatake bansan daliliba kodan kinason babanane Khadija tayi murmushi tace dama haka Allah yake ikonsa soyayya gamon jinice""labilata tashi zaune takurawa. Khadija ido kamar mainazarin wani abun saikuma tafashe dakuka data tunoda kudirin lubabatu akan Khadija Itama batasan sanda tafara kukanba suka hade kai sunata kuka akarasa Wanda zai rarrashi wanie Aisha✍🏼 [3/12, 9:25 AM] 1man: ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠ Chapter 85 By Gentle Lady💃🏽 Saida sukai mai isarsu sukadawo rarrashin juna""" labila tace zanyi kewarki sosai sahiba idan kikatafi khadija tace nima haka wlh sahiba Amman karkidamu ga wayanan ai zamudinga waya kodata daddy ce Nibandama wani Abu mezaihana kicewa daddy kema zaki wlh zanfi sakewa idan inaganinki"" labila tace naki wayon aiko nan gani nane yasaka kika sakankance gobe aurenki sati dayafa Amman bakitaba zuwa wajen mijinkiba saikace haka akacemaki anayin auren"" wlh kebandah wani Abu dasaina hadaki da inna airanarda za akawoki bahaka akace kiyiba Khadija ta marairaice fuska kamar zatayi kuka tace daddy nefa yace inbari yafadamaki kizo kirika tayani kwana kokuma haka kurum baikiraniba nidadi miji sai inkai kaina"" Labila tace ayya sahiba kinada gaskiya aibandauka hakan akayiba koni banbaki goyon baya kiyimasa rawar kafaba dole mudanja ajinmu irin namata aikingane dannafiso yagane akwai banbanci atsakaninku """ mudin bamasu arha bane Khadija tace kedai akeji wai mahaukaci yafada rijiya kinga kitashi muje muyi alwala dare yayifa sosai musamu ko hizifi uku mukaranta"" labila takalli agogon dakin yabuga shabiyu da kwata tace hakafa aiyau babu maganar barci hirar bankwana zamuyi Khadija tace nanfadai wlh saina kwanta kinsan bantabaa shiga jirgiba karnaje nayita kwasar barci ayimun dariya tayi maganar tana mikewa labila tace dariyadai waye zaimaki dariya Wanda ya aikeki bayankuma kowa da abunda yashamasa kai babu ruwan kowa dawanie Khadija tace to suda muje muyi alwalar tana dariya tatashi khadija tafarayin alwala sannan labila sukasoma karatu sai uku saurah suka kwanta Washe gari tunda sukai sallar asuba basu komaba sukahau shirya kayansu harda labila dantacemata itama kano zatawuce dazaran tarakasu Bayan sungama suka gyare dakin "" dasauran inda suka bata"" sukai wanka suka shirya sannan suka fita falon kasa Usman yanakusa da lubcy sai shagwaba takemasa kamar wata karamar yarinya shikuwa saibiyemata yake Haka kurum khadija taji wani iri aranta tayi saurin soke kanta ahankali labila tace kinga yanda akeyi itama data tsufa ballantana keda kike sabon jinie yanzu kike lokacin ganiyarki ta rayuwa Sam Usman baisan dazuwansuba lubcy ce kawai talurah kuma batadaina abunda takeba saima tayi tamkar bata gansuba"" Usman ne yaji kanshin khadija ya yawaita afalon yadago yakallesu dasauri yayi saurin saita kanshi yajanye lubcy daga jikinsa sosai yake jin kunyar labila Khadija tagaidashi bayan sunkaraso ya amsa cikin dakewar murya "" tagaida lubcy itama ta amsa labila tagaidasu sannan suka karasa saman dinner haryanzu Khadija batadago kanta sunyi ido hudu dashiba Tunda suka fara cin abincin yakeson tadago kanta danyakafeta damayun idanuwansa Amman taki dagowa dukda tanaji ajikinta yana kallonta Bayan sun kammala yakirah habu driver labila tafitomata da kayanta sannan takulle bangaren tarike key din"" lubcy ce tafitoda kayan usman driver yakwashe duka yasa mota suka rankaya dukansu Yace banga kindauko mayafinkiba kokina nufin iyah nan zakiyimana rakiya??? tana dariya tace inalaifi aiga yarkunan zata rakaku basainajeba Allah yakai lafiya yace Ameen Takalli khadija tace Amarya asha amarci lafiya khadija tasanne kanta dakansa yabudemata baya"" harzata shiga tadafe kanta"" innalillahi"" wlh nayi mantuwa Usman yace mantuwar me kumata dama haka shirinku yake kosati zakuyi kuna shiryawa karshe saikunje kunmanta wani abun Labila tace kabarta mana tadauko mekika manta??? Tace wlh littafaina da Qur ani kumafa dankar namanta Na ajesu kusa kusa Lubcy tayi karaf tace kekuma banda abunki Kanwata kudazakuje yawon amarci mezakiyi da littafai aikyabaridai harkudawo shima maigidan abashi lokacinsa Labila tace sabodame zatabàrsu dankawai zatayi tafiya sai akace kabar addininka agida kejeki dauko sahiba tamika mata key wlh kar shaidan yarinjayeki ko inakikaje rike ibada saikace dai su oi daba ta dauki addinin dakimaba"" khadija tawuce cikin gidan Lubcy tace aike komai saikin nunawa mutane kinfi kowa """ saikifadàman dawakike??? Labila ta marairaice fuska tace waini meyasa mom batasona daddy yanzufa dawata Yar makarantarmu nake tafashe dakuka Usman yace haba lubabatu yarkiicefa baidace kinamata hakanba"" tace alhaji kanajinfa abunda takefada itah yadace tayihàkà?? Nifa mahaifiyartaçe Yace aibadake takeyiba tafadamaki dawatà Yar skull dinsu take Bandama abinki aikinaji batakirah sunaba koda ma takirah suna tundakedai kinsan bahaka kikeba aishikenan saikibarta""" Tanisa shikenan alhaji yace yauwa kokefa yarnan dai takice komai lalacewarta nibansan dalilinda yasaka bakwason yayan fariba Ainikam hajiya batayimun irin yanda kikemata karfanaje nadawo nasamu kinhanamun ya rawar gaban hantsi"" labila tace aini dad wajen hajiya zankoma saikundawo zandawo Yace shikenan ma dama abdul sai Rigima yakewa hajiya waisaita kawoshi inda kike yauma naso turawa shima adaukoshi yadawo nan Tace idan yadawo dad karatun shifa ??? Daidai kawowar khadija yace kece kikasan hakan Amman wlh danaje kuka Yakama saiya biyoni nakawoshi wajenki"" shibaima tunanin kowa saike Khadija taimasu sallama suka amsa tamikawa labila key din bayan mota sukashiga shikuma dashi da driver suka shiga gaba tana tsaye tana daga masu hannu harsuka wuce sannan tajuya cikin gidan tana sake sake aranta sama tahau taduba inda ake ajemata sako tasamu layar wani murmushi tasaki tana juya layar labila kenan aiduk kame kamenki saina raba Usman da khadija saidai kuma kiyi hakuri Tasheke da wata mahaukaciyar dariya irin wacce *hatsabibin boka* yakeyi saida naja baya dannatsorata nadaukama shine yabayyana agabana"" Tunda suka shiga mota labila saizuba takeyi harsukakai airport sunsamu jirginsu Saura minti talatin yatashi Anan suka zauna zaman jirah duk abunda za ayi akagama lokaci yanayi suka soma shiga jirgi sai lokacin labila tasoma sharar hawaye tana kallonsu harsuka shige tana tsaye saida jirginsu yadaga tanasharar hawaye tana daga masu hannu"" Saida tadaina ganin jirginsu sannan tacewa habu suwuce ganin wani guy yanata kallonta"" tunda sukashiga motar tayi shiru sai sake sake takeyi aranta"" Sunakaiwa gida tace yajirata tashiga gidan lubabatu tana falo tayi sallama tahau sama tadauko jakar kayanta tasauko sannan tace ni mom zantafi Tanisa kigaishesu"" labila tace zasuji hartajuya saita tsaya tace nasan kinturah dad da sahiba Dubai ne akan wani mugun nufin naki kisani Allah yafiku kibarganin bokanki yanacin nasara kidauka komai kika nema aduniya zakisamu awajensa shikanshi damace Allah yabashi domin yayimasa takunkumi kiji tsoron Allah Mom kidaina biyewa wanann bokan tafashe dakuka maitsuma zuciya lubabatu tamere baki Idankundago kai tagado takalli indama labilar take saida tasakecewa please mom badanniba kidaina abunda kikeyi kinemi gafarar Allah Tadago takalleta ahankade tace kingama??? Labila tayi shiru tace totunda kingama nagode da nasiharki muna gaidasu tamike tahaye sama tabar labila tsaye Tabita dakallo saida tabace mata sannan tashare hawayenta tajuya taja akwatin kayanta Tafita"" habu yabude mata tashiga yaja motar akabude masu get sukafita" Fitarsu babu jimawa lubcy taciwo kwalliya tafita itama"" tashiga tanta tsetsiyar motarta akabude mata get tafita tasoma yawo cikin unguwanni kozata samu inda akeyin dahuwar abinci tunsafe har dare abunfa dawahala kuma ance karwani yaganie danhaka badamar tabawa wani kwangila dole dakanta zata binne"" Haka tayita yawo""" duk inda tatambaya daga masuyi dasafe saimasuyin da rana"" kuma tafison ahanya Dan agida tayiyu ba a cika wutar yanda zatayi zafie Su khadija kuwa tunda jirgi yatashi takankame idanunta kamar zatayi kuka sai addua takeyi hakan yasa usman yajawota jikinsa yakwantar harsuka lulaya cikin gajimare"" ahankali tasoma saukarda ajiyar zuciya ba awani dadeba tasoma barci maidadi asaman jikin Usman Dayalurah tayi barci yagyara mata kwanciyarta ajikinsa yarufemata fuskarta danbayaso ana kallonmasa puska tuni shima yasoma saukarda ajiyar zuciya yajingina kansa jikin kujerar jirgin yana tunani Lubabatu tana tsaka dayawo tabaro unguwarsu Danisa indama taje batasan sunan unguwarba bama tataba zuwaba wata yarkasuwace Dan kusa da bakin titi take komai anasiyarwa awajen wata maisuyar doya taganie da dankali da awara Tatsaida motarta tafito zuwa wajenta matar tanaganinta tawashe baki tanamata sannu dazuwa lubcy ta amsa suka gaisa tace nawa doya matar tace hamsin ashirin dankali kuwa goma biyar "" haka awara Lubabatu tace kullum kina fitowa??? Tace tomezaihana hajiya aizama gida banamu bane munada marayu agabanmu Lubcy tace Allah sarki aiyanada kyau kanemi halak dinka kamar dayaushe akesamunki anan??? Matar tace ai hajiya kaman karfe bakwai nake fitowa indorah koko idan yakare zuwa yanzu shabiyu nasoma suyar doya da dankali saidare nake tashi inbarwa yata inkoma gida inyi tuwon dare infito dashi Takwas muke tashi watarana harmunakai Tara"" lubabatu tace kainaji dadi bani doyar ta dubu uku kisa dankali Na dubu daya zandinga aiko driver na yana karbar Mani matar tawashe baki tace kaiii Amman naji dadi hajiya tanata wasar baki tazubawa lubabatu doyar tabata tafiddo kudi sabbi hull Tamika mata sukai sallama takoma motarta hartabar wajen matar tanadaga mata hannu saikallon kudi takeyi tana juyasu bayan lubabatu tayi nisa tatsayarda motar tafito da ledar doya dantasan koda tajeda itah gida bazata iyah cintaba danmaituyar doyarma kyankyaminta takeji tasoma rabon ido kozataga wasu almajirai tanakiran wani Yarugo kamar daga sama tajiii ance banda sadakaaaa aikinki zai lalace dasauri tajuya bayanta bataga kowaba tamiyarda doyar yaron yanazuwa tacemasa wanigida take nema kuma tagane tashiga motarta tawuce daniyar dadare zatadawo ta saka layar Aisha✍🏼 [3/12, 11:31 AM] 1man: *RAMUWAR GAYYA........ 💘* _Love story 50,50_ *Fertymerh Xarah* & *Ummy Aysher* 31 Shiru yayi yana saurarenta amma har lokacin bai ďaga kanshi ya kalleta ba, Jikinta yayi sanyi, she is not happy a yanda yake yi mata kamar xatayi kuka, ta qara marairaice murya, 'kayi haquri idan na bata ma, wallahi faruq is nothing to me Kuma ni bansan da xuwanka ba da baxan tsaya gurinsa ba, Ya tabe bakinsa haďe da ďaga kafadunsa ko ajikinsa, ya maida glass ďin sa ya rufe idonsa, ta ciki yake kallonta yaga duk ta damu, yaji daďin ganin yanda take bashi haquri tayi masa laifi, ya haqura amma yaqi ya nuna mata, Alawiya ce ta qaraso da textbook a hannunta ta miqawa khairi, 'ga book ďin ki gida xn tafi duk na tafi, khairi ta karba tana faďin, 'anjima xaki shigo, kitso nake son kimin, 'ban maki alqawari ba dan xn raka qawata biki amma idan mun dawo da wuri xn shigo, 'shikenan sai Kindawo, Alawiyya ta dubi sawwam, 'mutumin mu yau ba mgn ni naga yau sai wani daurewa kakeyi, yayi mata banxa, ta dubi khairi, 'meke damunsa, 'fushi yake dani, 'shine ni Kuma abin ya shafeni, to kayi haquri ko menene ka sassautawa qawata haka, Ya juya ga motarsa alamar xai shiga khairi taqi ta matsa, Alawiya ta fice tana dariya, 'haquri nake ta Baka kake min shariya haka, 'matsa xn shiga mota, ba musu ta matsa ta bashi guri ya shiga motar yaja ta a fusace tana tsaye tana kallonsa har ya fice daga Skul ďin, Jiki a sanyaye ta nufi hostel, baxata qara xubar da ajinta gurin bashi haquri ba har ya gaji da fushin ya sauko, Sosai ta damu, ranar duk a kwance ta jini jikinta sukuku hankalinta da tunaninta duk yana kansa, ko ringing wayarta tayi da sauri take dubawa ko shine idan ba shi bane sai ta cillar da wayar tana tsaki, wayar kowa bata amsa ba ranar kamar yanda itama bataji muryar sahibinta ba, Sawwam Kuwa har Ga Allah ya haqura, yayi mata Hakan ne dan ta gane laifinta sosai ta daina tsayuwa da wani, yana tsananin sonta da kishinsa baxai jure ganinta da wani ba, so a gobe xasu shirya ya nemi sulhu tunda yaga ta damu duk da itama yasan tayi fushi da shi tunda gashi bata nemesa ba, ba text ba Kira. Washe gari da sauri tayi shirinta ta fita lectures kasancewar 8:00am suke da lectures, Tana fita ta haďu da Alawiya xata shigo hostel sai suka wuce tare, 'shine kika qi xuwa jiya ko, kinbar ni dakai duk ya cunkushe, 'bamu dawo da wuri bane amma yau baxan je gida ba sai nayi maki, 'kinxo min da assignment ďina kuwa? 'yes yana jaka sai muyi submitting idan mun fito lectures, 'shikenan, suka shiga hall ďin, 10:00am suka fito lectures, bayan sun fito Alawiyya tayi gurin saurayinta, sai ta sami guri ta xauna cos xasu shiga wata lecture basu gama ba, kamar wacce aka ce ta ďago, tana ďagowa idanunta suka sauka akansa, yana tsaye jingine da motarsa hannuwansa sarqe a qirjinsa, wata budurwa ce a gabansa batasan ta ba yau ta soma ganinta, Jikinta ya ďauki rawa sosai hankalinta ya tashi, kada sawwam ya barta ne ya sami wata da Kuwa ta shiga uku yanda take mutuwar sonsa a ynxu takejin ba abinda xai iya rabasu, Suna haďa ido da sawwam tayi Saurin ďauke kanta, ta tattara kayanta ta tashi daga wurin ta shige hall inda sauran friends ďin ta, Sawwam yayi murmushi yana kallonta, 'kingane farida, Suhaib wani irin mutum ne mai wuyar al'amari, dole sai kina haquri dashi amma duk da haka bai kyauta ba xn mishi magana, Tace Nagode sawwam, ina mutuniyarka yau duk ban ganku ba, 'ita nake jira ma anan inaji bata fito lectures ba, tayi murmushi, 'kuna birgeni dama haka Suhaib yake dana dace, 'kinma dace abokina fa First Class ne matsalar shi ďaya Kuma xn mashi mgn xai gyara, 'Nagode sosai ta juya ta fice, ya jingina yana jiran khairi yasan tayi fushi a ynda yaga fuskarta, Wannan Karon lecture ďin da akayi komai bata fahimta ba duk hankalinta da tunaninta yana gurinsa gani take har ynxu yana tare da wannan budurwar, Sun fito lectures Alawiya tace kije gani xuwa, man bai gaji da gani na ba, Murmushi tayi kana tayi hostel fuskarta a ďaure ganinsa tsaye, inda yake ma bata kalla ba, ganin da gaske take yasha gabanta, 'kin ganni fa shine kika wani fuske, tun ďaxu Ina jiranki ingayamiki na haqura shi kenan komai ya wuce, tabi ta gefensa xata wuce ya qara tare ta, 'Ni ynxu Kuma menayi kike fushi dani, Takaici na qara rufeta tambayarta yake meyayi bayan yasan abinda yayi, ta qara bata fuskarta taqi ma ta kallesa, 'Ni ynxu koma menene kiyi haquri sulhu naxo muyi Kinsan banda wacce tafiki fa ya faďa cikin xolaya, harara tabisa da Ita kamar kwayar idonta xata faďi qasa, 'ita wacce nagan ku tare fa? 'au na manta... taja tsaki ta fice yayi saurin riqo hannunta, *'Ramuwar gayya* ce da gangan nayi dan kiji yanda naji jiya dana ganki da wani, tunda kinji ynda naji shikenan, _50,50_ kiyi haquri, Tayi shiru tana kallonsa, batare da ta tankaba, 'budurwar Suhaib ce fa, mun fito lecture take gayamin abinda ya hadasu shine na jawota nan Muna mgn dan kigani, ni ynxu bama Wannan ba, abar mgnr, fushin ma kidaina nima na daina, Alawiya tayi maki kitson? Kamar baxata tanka ba sai Kuma ta girgixa kanta, 'muje saloon ayi maki acan bnga alamar ta iya kitso ba fa, 'ta iya ita kemin ai, ynxu ma xataxo tana hanya, ya sauke ajiyar xuciya, 'idan tayi ki dauki pic ďin ki turomin ta whatsapp ingani inyayi kyau, dama ga gashin ba fasali, Ta saki murmushi tana kallonsa, 'Kuma a hakan wani ya gani yace yana so, 'to ya xanyi tunda Ina son kayana, da haka suka bige da hira har Alawiya taxo itama tasa bakinta kana suka nufi hostel yayi gida. *pherty xarah💞* & *ummi shatu👌🏼* [3/12, 11:43 AM] 1man: 🔮```BAZAN BARSHI BA!```🔮 🔮🔮🔮🔮 *```Page 69```* Hawayenta ne yaji suna sauka a hnkli kan qirjinsa ya kira sunanta a hnkli bata tanka shi ba ta qyale shi sbd wahalar da take ciki ko magana ma bata son yi don sae taji kmr yaune ta soma sanin d'a namiji a rayuwarta don wani irin mugun zafi take ji a qasanta har bata son tayi wani motsin kirki. Mohd kuwa sae kallon ta yake cike da tausayi don shi kan shi yasan ya bata wahala ba kad'an ba. Ya sake kiran sunanta a karo na biyu bata tanka shi ba sae kuka da ta soma yi cikin dasassiyar muryar ta da tasha kuka. Wacce duk ta tattara zanin gadon ta rufe jikinta dashi sbd wutar da aka jima da maidawa bcs dama ba wutar gari ce aka d'auke ba daga laifin mitar gidan ce. Man yakai hannu ya rage hasken d'akin snn ya nemi cire mata zanin gadon amma ta kama ta rirriqe ta hana shi cire zanin bai takurata ba sae d'aukar ta da yayi ya nufi bathroom da ita wacce tasha kuka ba kad'an ba don wanka ya mata kan dole ya kuma gasa mata jikinta sosai snn ya fito da ita ya kwantar kan bed sae kuka take marar sauti har tayi bacci. Mohd dake zaune can gefe guri d'aya ya sauke numfashi had'e da matsowa gab da ita ya kwanta tare da jawo ta zuwa qirjinsa ya rungume yana ta kallon fuskarta dake masa mugun kyau idan tana bacci, a hnkli ya d'aura lips d'insa kan goshinta ya mata kiss yana mae ci gaba da kallonta cike da so daga haka ne shima bacci ya kwashe sa sae safe. Washe gari mohd ya riga Ryynt tashi yaje bathroom ya d'auro arwala yazo ya sameta ta farka amma bata tashi daga kwancen da take ba sae hannun ta da take d'an moving dashi kan bed , ya durqusa gab da ita had'e da riqo hannunta yana mai kallonta cike da tausayi bata kalle sa ba sae hannun ta da ta janye taje zuwa share qwallar da suka zubo mata ya riqe hannun ya kai nasa hannu ya share mata qwallar had'e da fad'in "yi hqr tashi kije kiyi arwala kizo muyi sallah kinji" Shaye da toka ta kalle sa kawae ba tare da ta iya ce masa komai ba don kanta ke mata masifar ciwo a gurin ga zuciyar ta dake ta faman tashi,ba'a fi minti d'aya ba ta miqe lokaci d'aya ta tafi da gudu zuwa bathroom tana kwara amai ta samu da qyar aman ya tsaya mata mohd dake riqe da ita shi ya taimaka mata ta wanke bakinta ta d'auro arwala snn suka je sukayi sallah ko shi a daddafe tayi sllr wacce tana idarwa sae kwanciya tayi kan darduma mohd dake addu'a kallonta kawae yayi yaci gaba da addu'ar sa da ya gama ya tashi yaje ya bud'e fridge ya d'auko gasasshiyar kaza yaje ya mata warming sae gashi ya dawo d'auke da fresh milk a cup da kuma naman kazar da ya saka a cikin plate. Yazo ya durqusa gab da ita yana kiran sunanta a hnkli bata tanka shi ba don har bacci ya kwashe ta a lokacin shi kuwa bae kula da hakan ba sae zama da yayi tare da janyo ta zuwa jikin sa ya cire mata hijab nn ta soma kuka dan sae a lokacin ta farka ya kira sunanta a natse yana ta6a jikinta da yaji ya soma yin zafi bai ji dad'in zafin jikin ba dan sae yaji damuwa a ransa. Ryynt dake kan jikin sa sae qoqarin zamewa take ta kwanta kan darduma bai barta ba sae qara kwantar da ita yayi kan qirjinsa ya d'ebo naman kaza zae bata tayi saurin girgixa kanta alamar bata so ya ajiye naman ya shiga rarrashinta kan tasha ko fresh milk ce nn ma taqi kan dole ya barta ta koma kan darduma tayi kwanciyar ta bata jima ba bacci ya koma d'aukar ta. Baccin qwarai tayi dan ba ita ta farka ba har sae da akayi sllr zuhur ta tashi a daddafe dan har lokacin bata jin dad'in jikinta taje tayi wanka ta fito ta nemi er doguwar riga ta saka snn ta sanya hijab tayi sallah a nn gurin tayi kwanciyar tana d'an jin tashin zuciya nn ta lumshe idanunta a hnkli sae ga man ya shigo d'akin tana jinsa tayi kmr bata san da shigowar sa ba shi kuma yayi tsaye yana kallon ta d'auke da kular abincin da ya kar6o a gurin su Amir dan duk cikin gida d'aya suke kowa dae da nasa 6angare. Kan dining yaje ya ajiye abincin snn ya d'auki breakfast d'inta dake ajiye tun d'azun ya fita dashi dan yasan yanzu kam lokacin cinsa ya wuce sae dae kuma lunch. Bai wani jima ba ya dawo ya same ta kmr yanda ya barta wanda duk a tunanin sa bacci take. Ita kuwa tana nn kwance cikin jin jiki har akayi sllr la'asar,yayinda man ke zaune sae kula yake da duk wani motsi nata. Ganin anyi sllr la'asar ne yasa yaje yayo sllr ya dawo ya sameta itama tayi sllr tana zaune kan darduma ta had'e kai da guiwa tana fama da kanta dake mata masifar ciwo. Yazo gab da ita ya durqusa ya shiga kiran sunanta a natse tayi kmr bata ji sa ba don ko magana bata son a mata. Nan ya tashi ya d'ebo mata abinci ya kawo gabanta ya ajiye yace cikin muryar rarrashi "yi haquri kici abinci dan Allah kinga tun safe komai baki ci ba kinji" Rynt kam qamshin abincin soma damunta ma yayi nn take taji cikinta ya hautsine ta soma yunqurin amae bai bar ta tashi ba ya riqe ta dan yasan ko taje wahala kawae zata yi dan ba wani abu taci ba,nn ya kwantar da ita kan qirjinsa yakai hannu yana shafa bayanta yayinda ta cusa fuskarta gabad'ya cikin qirjinsa tana shaqar qamshin turarensa da ya soma kwantar mata da zuciya daga haka ne bacci ya kwashe ta sae kallon ta yake cike da tausayi dan yasan dole tana jin yunwa gashi jikinta har yanxu yana d'auke da zafi. Yana nn zaune abinshi rungume da ita sae bacci take ya soma jin zafin jikin nata sae qaruwa yake musamman kan goshinta nn ya d'auke ta yaje ya kwantar kan bed ya jawo wayar sa ya kira Amir ya gaya masa irin magungunan da yake buqata. Ba jimawa yaji knocking yaje ya bud'e qofa, Amir dake tsaye a bakin qofar yace"inace dae jikin da sauqi koh? Mohd yace"to jikin nata sae zafi yake tayi tun safe har yanzun wlh gashi tana fama da yunwa don tun safe komai bata ci ba yanzu da na kawo mata abinci ko qamshin sa ma bata son ji bare ta iya cin sa. Amir ya nisa tare da fad'in"bari naje to nasa my wife ta mata farfesun kifi ko zata iya cin sa" Mohd yace"olryt tnks" snn ya kar6i ledar magungunan da Amir ya miqa masa ya maida qofa ya rufe yaje ya ajiye ledar magungunan kan bedside drawer ya zauna jiki sanyaye kusa da Ryynt yana kallonta cikin tsabar tausayinta da yake ji don kallo d'aya zakayi mata kasan cewa tana jin jiki. Bata wani jima da baccin ba ta farka sae juyi take tana neman fad'owa kan gadon mohd da ya fito daga bathroom yaxo da gudu ya tarbota, ta dafe kanta dake mata masifar ciwo har bata son bud'e idonta sae hawaye kawae dake fitowa a idanun nata. Fuskar sa d'auke da tausayi yakai hannu yana share mata hawaye snn ya jawo farfesun kifin da mtr Amir ta kawo mata tana bacci. yana bud'e kular farfesun kifin knn, taji tashin zuciya sosai bakinta ya cika tap da yawu ta tashi aguje ta nufi bathroom tana kwara amae mai wahalar gske dmn amman kumallo ne kawae, tana gama amman ta samu da qyar ta wanke bakinta sbd wani irin jiri da ke d'ibar ta ga ciwon kai kuma. Mohd ya riqo ta zae taimaka mata su fito bathroom d'in ta zame jikinta a hnkli ta zauna qasan tiles d'in bathroom d'in ta had'e kai da guiwa sae numfashi take fitarwa a wahale. Mohd dake durqushe gabanta yana kallonta kmr ya cire ciwon yake ji ya maida jikin sa. Cikin damuwa kmr zae yi kuka yace"Ryynt yi hqr tashi muje ki d'an ci wani abu sae kisha magani kinji" Da qyar murya can ciki tace"um um bazan iya cin wnn farfesun kifin ba ka fita dashi dan Allah" Mohd yace"shike nn idan na fitar me kike son a kawo maki kici to" Cikin muryar kuka tace"nima ban sani ba kawai kaje ka fita da farfesun kifin tukun" Nan ya kalleta snn ya tashi yaje ya d'auki farfesun kifin ya fita dashi wanda ya d'an jima kafin yake dawowa d'auke da ledar snacks a hannun sa yaga still bata fito daga bathroom ba yaje ya sameta kwance qasan tiles har ta koma yin wani bacci kuma, ya d'auko ta ya fito da ita ya kwantar kan bed. Yayi zaune gefen gadon had'e da dafe kansa don ko kad'an bae so ta koma yin baccin ba har sae ta d'an samu abinda taci ta kuma sha magani tukun. Ba ita ta tashi daga baccin ba sae bayan isha'i ta tashi cikin kukan wahala dan wata irin yunwar masifa take ji ga jikinta da mugun zafi har ita kanta bata son ta6a jikin nata. Mohd dake zaune tun d'azu zaman jiran farkawarta ya janyo ta a hnkli zuwa jikin sa yana share mata qwallah had'e da rarrashinta, ta qara narkewa sosai a qirjinsa murya can ciki tace"zanci abinci" Jikin sa na rawa ya jawo kular abincin su da aka kawo musu na dare ya d'ibar mata abincin a plate ya d'ebo a spoon zae kai bakinta ta kalli abincin kawae ta kauda kai,snn ta kalle sa qwalla tap a idonta kmr zasu zubo tace"kayi hqr dan Allah ni bazan iya cin wnn abincin ba idan da abun sha ka bani" Jiki sanyaye ya maida abinci ya ajiye snn ya jawo pillow ya kwantar da ita don ya fhmci ko zama bata iya yi. Ya tashi yaje ya bud'e fridge ya tsiyayo mata fresh milk ya kawo mata had'e da snacks d'in da ya siyo mata a d'azun ya shiga bata da kanshi ta d'anci ba sosai ba sae fresh milk da ta d'an sha rabin d'an qaramin cup tace zatayi sallah ya bata magunguna tasha snn ya ja hannunta zuwa bathroom ya taimaka mata har wanka tayi snn tayi arwala suka fito . Tayi sallolin da ke kanta wacce da qyar taga ta kammala sallolin sbd har lokacin kanta kamar zae tsage take ji amma ta fara jin qarfin jiki dae dae gwargwado sae dae a kwance tayi addu'a dmn in ta kwanta ciwon kan na d'an mata sauqi. Mohd yazo ya sameta gurin ta kammala addu'a ya riqo hannunta tare da fad'in"zo muje to na kaiki kan bed ki kwanta koh" Komai bata iya ce masa ba har ya tallabeta cak sae kallon sa take tayi har yaje da ita kan bed ya kwantar. Billy giro😊 🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮 ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠ Chapter 82 By Gentle Lady💃🏽 Ahankali tatako inda yake Amman bata zaunaba hannunta yajawo yayi mata mazauni akan cinyarsa kanta yanakasa tana wasa dayatsunta Yadago fuskarta ahankali yace Deejarh na meyasa bakason kallona ne kodai fuskata tsoro take baki??? Kara sanne kanta tayi tana girgiza kai yace nibanji mekika ceba magana zakiyi"" ahankali tace ah ah"" yace inhakane saiki dago ki kalleni Ahankali tadago takalleshi idanuwansu suka sarke Dana juna kowanne zuciyarsa bugawa takeyi kamar ganga""" dasauri khadija tasanne kanta bata iyah jimirin kallon cikin idonsa yanayimata kwarjini sosai sake dago fuskarta yayi wannan karon idanuwanta alumshe suke hakan yabawa Usman damar sunbatar labbanta Yadaukesu tsayin mintuna ashirin yana wasa da itah ko bihim bataceba kuma batayi yunkurin hanashiba dankansa yagaji yasaketa yajingina kansa saman kujerar yana maida numfashi""" Haryanzu tana nan indatake sai saukarda ajiyar zuciya take ahankali"" yadade kwance saidayaji yasamu natsuwa sannan yadago akasakalance yace kinci abinci kuwa??? Kaitagirgiza alamar ah ah Yace to tashi kihadamun ruwan nayi wanka kobashi kikazo tayaniba"" batace komaiba tamike zuwa toilet din tayi addua sannan tashiga tahadamashi"" ruwan tanacikin toilet din bata fitoba harya gama cire kayansa"" yasameta toilet din Yace waiharkin hada shine bakizo kinfadamunba kika tsaya anan kodai wankan zaki tayanie??? Cikin zolaya yayi maganar Aikuwa zumut tafito tace ah ah ba amfanie a aje ruwane abayan gida afita saboda shaidanun aljanu sunayin wanka aciki kaikuma idan kashigo bakaganin sauyin komai saikayi wanka dasu hakan yanajawo safuwar jinnu dakuma cututtuka da shaidanun aljanu kan iyah jefar mutum dasu Kaiyagyada alamar yagamsu """ yashiga ciki tareda addua yarufe ko far wajenda yake ajiye kaya tabude tarasa kalar kayanda zata daukar masa shiru tayi tana nazari Wadansu kananun kaya taciromasa jar rigace da bakin wando "" rigar tanada dogon hannu tayita juya kayan waikomadai bayason kananun kaya??? Farar singlet tadora masa Saikuma ta aje tafesamasu tirare wayarsa tadauko tashiga massage tayi rubutu ta aje saman kayan tafita falon tazauna jiransa Bayan yafito wanka baisameta dakinba yaga kayanda taciromasa wayarsa dayagani da haske yadauka Bansan irin kayanda kakesoba nafitomaka dawan nan idan basuyiba saika sauya"" murmushi yayi ya aje wayar yashirya yasaka kayan rabonsa dayasaka kananun kaya haryamanta"" yataje sumarsa yagyara dankaramin sajensa saiyafito a Usman dinsa Murmushi yayi lokacinda yakalli madubi yagirgiza kai wayarsa yadauka yasaka agefen aljihunsa nawando yasa daya abaya sannan yafito Tunda taji kamshin turarensa tadago kanta tadauka baisaka kayanba saitaganshi sanye cikin kayan yayi masifar kyau tayanda khadija takasa boye kunyarta takuramasa ido cen kasan makoshi tace masha Allah tsarki yatabbata ga ubangijinda yahalitta wannan surar"" tsaye Usman yayi agabanta yasaka hannunsa daya acikin aljihunsa yana sakarmata murmushi Jinkamshinsa"" gab da itah yasaka tadawo daga duniyar tunaninda taje""yace Deejarh na nayimaki kyaune??? tagyada kai saiyanzu tadanji kunya murmushi yayi yashafi gefen fuskarta yace muje muci abinci yunwa nakeji batace komaiba suka jerah zuwa kasa Lubabatu da labila suna zaune saman dinner sukawai sukejirah kusan tare suka kallesu yanda sukajero sunyi kyau Sundace dajuna Usman yadawo kamar danshekara ashirin dabiyar Wani mugun kishi lubabatu taji waidama haka Usman yakeda kyau??bata taba ganin shigarda taburgetaba irin wannan Harsuka karaso batasan sun kawoba saida khadija tace mata inayini"" tace uyum lafiya qalau Amarya anyinie lafiya qalau tace sannan suka zauna lubabatu tazuba wakowa saita hadewa labila da khadija sukasoma cin abincin labila kam dadi kamar yakasheta kobakomai tasan yanzu dadyn ta yasamu matarda yadade yana nema kuma insha Allah babu abunda zaisamu sahiba"" wajen yayi shiru bakajin motsin komai sai karar cokullah kowa da abunda yake sakawa aransa"" bayan sun kammala"" Usman yamike yana kallon agogon hannunsa yakalli lubabatu yace yau Abdul zaikoma tundazu inataredashi yanzun ma nadawone inyi wanka saboda zafie Tace habadai harzasu koma bazasu jirah suyimana ko sati dayaba??? Yace kinsan akwai aiki sosai idan zaiwuce zaikawo madam kugaisa nizanje kano yanzu"" tace to Allah yakiyaye yakalli khadija yace kina bukatar wani abun??? Kaita girgiza alamar ah ah yace shikenan sainadawo tace adawo lafiya Allah yakiyaye yace Ameen sannan yawuce Labila tahau zungurarta tana nokewa saboda lubabatu tana wajen abun yabawa labila haushi ta mike taja hannunta saida takai bakin kofar tace saiki wuce khadija takalleta saitaga tana harararta tasakai tafita itakuma tajuya takoma cikin falon tazauna tana kallon wayarta kamar batayi komaiba Lubabatu kuwa binta kawai takeyi dakallon mamaki watoma itah yarinyar tanada kunya dakuma kawaici yartane batasanshiba lallai dole taraba tsakaninsu wanann shegiyar abotar dole abarta"" 🙄 Usman yana bude mota zaishiga yahangota tajikin glass murmushi yasaki danyasan aikin labilane Dan indai Dan khadija yanda takeda kunya bazata iyah tasowa agaban lubabatu ba Tanakawo wa wajen yasoma dariyarta ganin ta shake kamar zatayi kuka yanzu idan takoma dawanne ido zata kalli mom itah gata marar kunya hardawani zuwa rakiyar mijie Yace menene Deejarh na??? Tace bakomai motar yabude yace tashigo ciki babu musu tashiga yace naga kamar ranki abace kokinazuwa inje dake??? Murmushi tayi tace sokakeyi Yayana yadakeni??? Yace akan mezaidakeki bayankuma kinataredani Tace tabdi wlh bakasan halinshiba aizaice yaushe aka kawonie harnafara yawo idan kaje kakarbomun wayana wajen inna namanta bandaukotaba"" yace shikenan yasunbaceta akumatu yace sainadawo tace adawo lafiya tafita tarufemasa motar tana tsaye saida taga wucewarsa tajuya tàkoma fàlon kanta yanakasa tashiga da sallama Labila ce ta amsa cikin jindadi kusa da itah tazauna idonta haryanzu yana kasa abunyabawa labila dariya tahau yimata dariya saida taga alamar zatayi kuka sannan tadaina tace sorry small mom bazansakeba ayimun murmushi mana Khadija takaimata duka tagoce sukahau dariya lubabatu tanagefe tana kallonsu mikewa tayi tace labila kizo inason ganinki tawuce zuwa sama Labila takalleta takalli Khadija batace komaiba harkusan tsayin min tuna goma da tafiyarta sannan khadija tace waiba kiranki mom tayiba naga bakida niyar tashi Tanisa sannan ta mike tace tashi muje"" harararta tayi tace bangane intaso mujeba kikasan kiranda mahaifiyarki takemaki kijemana kinsan akwai sirri tsakanin uwa daya"" Labila tace tonidai idan bazakiba nima zamana zanyi"" khadija tace au ashefa badadi tokizauna Amman wlh nima duk kikasake cewa inje wajen daddy idanhar batare zamujeba nima bazaniba tamurguda mata bakie Labila tawaro ido tasan khadija zata aikata hakan tace rufamun asiri nidanakeso asamamun Kanwa barito naje nidai tawuce tana dariya""" khadija tace Allah yashiryaki sahiba Da sallama tashiga ban garen lubabatu tana saman kujerah ta amsa sallamar kasa tazauna tacemata ganie lubabatu tayi murmushi tace saiyanzu saiyanzu uwartaki tabaki izinin zuwa tundazufa nakiraki Kanta yanakasa tace karki daukarwa kanki wani hakkin wandama yake kanki ya isheki ni sahiba batahanani zuwaba hasalima banyi niyar zuwaba itah tasakani dole Danbakyau kisamu mutum biyu sunafirah batareda kinnemi izinin ganin dayanba kijadaya agefe wani abuñ zaitaba zuciyarsa Haryayi tunanin kodai maganarsa za ayi lubabatu tamere baki tace wannan kuma kutashafa tayi shiru nayan dakiku sannan tace labila inaso kifadamun mewannan yarinyar tafini dashi dakike sonta nibakya sona karfa kimanta Nice nahaifeki duk wani Wanda zakiso yasoki bayana yake Labila tayi murmushi tace kwarai mom nasanda haka nima inasonki irin sonda ya takeyiwa nahaifiyarta halayenkine banaso saboda sun kasance ababen kyama Kinsan makomar Wanda yakashe musulmi kuwa??? Bayankuma alhakin daddy dakike dauka idan harxaki watsarda miyagun halayyarki wlh zanbaki mamaki danzandawo tamkar kare agaban sugabanta Lubabatu tamurmusa tace ke yarinya ce labila haryanzu kuruciya tana cinki nifa gatane nakeyimaku amatsayina Na mahaifiyarku banaso kobayan ran mahaifinku Ku tagayyara Labila takalleta da mamaki tace kekintaba tunanin mutuwarki??? Gaban lubabatu yabada rasss hartaruntse idonta Kokintaba tunanin wannan dukiyarda dady yatara bazata kareba??? Ai ahaifi da da arzikinsa yafi amutu abarmasa gado duniyar nan dakike ganie bafa matabbata bace koshi bokan naki yafadamaki shibazai mutuba wlh boka makaryacine mom yanaso yabatardakene dake dashi idan har kuka mutu Baku tubaba wutace makomarku kiwatsarda duka abunda yabaki kidogara ga Allah shine zaibaki duk abunda kikeso Afusace lubabatu tamike tayanka mata mari tace rufemun baki shashasha wacce batasan maisontaba tunkafin. Ahaifeki nakejin irin wannan wa azin ga malamanda suka keceki awajen karatu Amman kokadan baiyi aiki akainaba sai wanann maganar taki kedabanda bokana harma za ahaifeki kekanki darajarsa kikeci wlh Labila tadago cikin kuka tace wlh karyane nibabu wani kazami mushiriki daya isah inci darajarsa shaidan kawai inna kintata daidai dadyna bama cikin hayyacinsa ya aurekiba kaico ni labila meyasa mahaifiyata tazama haka daga ina matsalar take??? Lubabatu tace tashi kibacemun daganie kuma nasan duk take takenki wato ke gamai Kawa?? Nibabu ruwana da kawancenku idankuma baki fita sabgataba harke zansa agama dake dannalurah kinashigarmun hanci nagaji da abunda kikeyi kinsoma shiga huruminda banakiba Labila tasaki murmushin takaici tace kisa yakasheni mom saimuga idan agurinshi rayuwata take nikoda mutuwa nayi wlh banda takaici me akeyi dawannan kazamar duniyar maitattareda da dauda da kazantar masu halayya irin taku dake da bokan naku sainaganie idan kudin zaku gujewa mutuwa "" ta mike hartakai bakin kofa tace kiyi hakuri mom banason muryana tana zarta taki awajen magana kigafarceni Allah yaganardake gaskiya tabude ko far tafita anan tabar lubcy tsaye rayuwarta intayi dubu tabaciii kirjinta kamar zai balle kofar dakin takulle tawuce kuryar dasauri danfa dole *hatsabibin boka* yasan matakinda zaidauka akanta Aisha✍🏼 ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠ chapter 83 By Gentle Lady💃🏽 Dasauri takarasa wajenda ta ajiye akwatin madubinta tadauko tafito dashi tashafa tareda kiran sunan *hatsabibin boka* saigashi haske yayi tartsi saigashi ya bayyana saman kujerarsa idanuwa jajir lubabatu tasoma magana Haba boka waimeyasa hakan Ashe akwai lokacinda zanga irin wannan ranar yata tacikina tana nema tafi karfina??? *hatsabibin boka* yakece dawata mahaukaciyar dariya yace babu abunda banganiba acikin madubin tsafie na kisani wannan aikin bakaramin aikibane dole kirabasu indai kinaso kiga karshen wannan yarinyar Cikin damuwa tace yazanyi inrabasu boka??? Kaima kasan labila idan tanason mutum bazata taba barinsaba dama batasan shirina akantaba dasauki Amman yanzun bazata taba yarda inrabasuba Yasake kecewa da dariya yace cikin sauki zakirabasu tace taya kenan boka??? Yamurmusa kicewa mijinki yakamata suje yawon shakatawa kodan sumore amarcinsu tunda kinlurah Amarya kunya takeji bazata sake jikinta ananba Lubabatu taware ido tace habadai idan nayihaka anya banyi wautaba??? Wata razanannar tsawa yadakamata yace nifa ba amusu danie dazaran nace ayi kaza kar atsaya yimun musu idankuma bahakaba narantse dagirman tsafina bazanji tausayinkiba wajen nunamaki kuskurenki Tuni jikin lubabatu yahau kyarma kamar mazariii tadukadda kanta tubanake yakai wannan gawurtaccen boka man tawa nayi Amman zankiyaye gaba Batareda ya sauraretaba yace idan kin aikata bayan suntafi saiki nemenie yabace battt yaufa lubabatu tabatawa boka raiii jitake gabadaya duniyar tayi mata zafie kamar wutaa jin Kamar ana kwada sallama yasaka tamiyarda komai tashiga toilet tawanko fuskarta tadan goga powder tafesa turare sannan tabude kofa tafita matar Abdul ce tana ganinta tasaki fara a tace karaso mana Hauwa u"" koda yake nayi fushi tunsanda kikazo sunan Abdul bakisake zuwaba karasawa tayi cikin falon tazauna tana dariya tace haba Anty luba kinsan balaifina bane wlh tunsanda mukaje minna bansake dawowa nan ba dadyn ameer ne kawai yake zuwa koshi bayawuce kwana daya kema kinsan danazo aidole inzo nandin saboda ke Lubcy tace hakane ina yaranki ainasan yanzu kinyi haihuwa biyar ko??? Hauwau tarike baki tace lala Anty luba kebakiyi biyarba saini kanwarki"" lubabatu tayi dariya tace aimu munbarmaku bakiga Dan autana yagirmaba Hauwa u tace inazanganshi labila kawai naganie ai"" nima haihuwana uku biyu mata daya namiji Asiya kausar sai Muhammad inakiranshi ameer dansunan babane"" lubabatu tace masha Allah Allah yarayamana su tace Ameen bari nasa akawomaki ruwa""" Ah ah dakinbarsu labila tabani ruwa wlh tundazufa mukazo su asiyama sunakasa nabarsu"" tace shikenan ya minnar??? Tanacire mayafinta tace Alhamdulillah ai inasaran kwanan nan zandawo garin nan nagaji dazaman cen bansan kowaba saidai makota ko anawani Abu saidai kaji labari nacemasa yayi aure kawai saiyaje da amaryarsa nikuma inzauna dani da Yayana Kallon wata marar wayo lubcy taimata tace lallai Hauwa wasu suna gudun kishiya kekuma harnemanta kikeyi??? Tace to menene Anty luba arzikinefa ai abun farincikin kine mijinki yakara aure alamun kunada wadatar zuci kenan ni wlh koda hudu zaiyi inaso kowafa da halinta zata zauna nasandai duk inda zaije yazagayo kaina zaidawo dannice uwargida kingakuwa girmana bazai taba faduwaba kobayan raina za adinga yabamun insamu kyakkyawan shaidu aduniya yafi inmutu inbarwa Yayana abun fada Tuni lubcy tadauke wuta kardai hauwau tasan abunda nake aikatawa??? Takatse mata tunani dacewa amaryarki taburgeni wlh gata karamar yarinya zakuji dadin zama dajunanku dannalurah saitayi hakuri Lubabatu tace hakane kam wlh ai inata addua dadyn labila yayi dace kinsan matan yanzu sai ahankali watama kina zamanki lafiya damijinki dazaran tashigo saitatashi rabaki dashi Matanda yake aurah duka banakwarai bane Amman wannan kam ina tunanin andace!" Hauwau tace hakane dadyn ameer yasanardani ai Allah yasake shiga tsakaninmu da mugayen mutane lubcy tace Ameen Mikewa Hauwa tayi lubcy tace waiharzakiyi me??? Tana yafa mayafinta tace tafita mana kinsanfa jirgi bazai jiramuba dole mujirashi dalokacin tashinsa yayi zaitashi tace hakane tamike turarukka dakayan shafawa tahado mata suka sauko kasan sun samesu sunata firah kamar dama sunsaba dajunansu duk Asiya tace kunga har mom tafito tonidai Anty kibamu number muyi chat Labila tace wlh bata chat saidai kuyi waya kuma banama tunanin tazoda wayar inaji tamantata agida saidai inbaki tawa Tace shikenan suka karbi number labila lokacin har su lubcy sun kawo wajensu tare sukai masu rakiya harkofa saida sukaga tashin motarsu sannan sukadawo Daki suka wuce kaitsaye danyin sallar la asar bayan sungama sukai zamansu adakin"" lubabatu Sam takasa jinta daidai tun abunda tayi yazama dole tasake kiran boka tabashi hakuri hakan kuwa akayi tasake kiransa tabashi hakuri yace ya yafemata Amman kartasake aikata irin wannan kuskuren tace tagode zatakiyaye Yace nasan abunda kike tsoro kisani babu abunda zaishiga tsakaninsu duk abunda yakefaruwa dasauran matansa itama aikin yashafeta muddin yayi niyar hada shinfida da itah zaisamukansa yana kyamarta saboda warinda zatarikayi kamar mushe Dazaran sunbar kasarnan zakiga laya a inda nasaba aikowa a ajiye maki kije kisamu wajenda kikasan kullum sai anyi dahuwar abinci tundaga safe hardare"" saiki tona murhun kisaka layar karkibari kowa yaganki dazaran kinyi haka kingama komai Yanda kikasan zafin wuta idan kikaje kusa da itah haka jikinsu zaiyi zafiii dazaran sun kusanci junansu zasuji kamar zasukama dawutaa dole su nisanci juna tahakan hankalinta zaitashi tadaina samun lokacinda zatazauna tayi addua saboda tunani alokacinne zamucika aikinmu akanta. Wayyo dadi tuni dadi yalullube lubcy tahauyimasa godiya yace maganar labila tabarkomai ahannunsa shiyasan yanda zaiyiii Tayi masa godiya tace zaiga sako aranar ta siye dabbobin ta aikamasa"" cikin kwana biyu tasamarmasu biza dakomai dantasan inhar cewa tai sutafi labila tana iyah cewa saitabisu wannan dalilin yasaka taiwa tufkar hanciii Aisha✍🏼 ☠ *HATSABIBIN BOKA!!!*☠ Chapter 84 By Gentle Lady💃🏽 Zaune suke dadare suna cin abinci lubabatu tace nikuwa yau akwai maganarda nakeso muyi dakai""" yakalleta yace Allah yasadai lafiya ??? Tarausayarda kai tana kallon khadija cikin fara a tace insha Allah baridai mukarasa cin abincin"" yace nidai kifadamun yanzu kinsanni da zumudi kamar sabon angwo gabadaya suka kwashe da dariya harsu labila"" Yace tokokunga laifina ninafison idan za afadamun Abu kawai afada yanzu kafin mugama bakisan iyah jaye jayenda zuciyata zatayiba""" adaure afadamun Cikin siririyar muryanta tace daddy kasanfa ba amfanie ana cin abinci ana magana kamar bakabawa abincin mahimmanciba""" yakalleta gaskiyarkifa Deejarh tobari mugama yayi maganar yana kallon lubabatu murmushi kawai tayi tacigaba dacin abincinta Aranta tace wannan hartasoma tafi labila iyah yi shi abincin harsai anyiwani girmamasa 🙄"" tsaki tayi aranta tacigaba dacin abincinta"" bayan sungama sannan yakalleta yace karfa kice naciga zanzari nasan duk abunda zaifito bakin nan naki alkhairine murmushi tasaki har hakoranta suka fito tace ko??? Yace koma zakice ainidanake dake nasan haliinki fiye dake kanki""" labila kam murmushi tayi aranta tace kadaisan Wanda kasani amman babu Wanda yasan halin mom sai Allah nda yahalicceta""" Tace hakane abunda yake gefenta tadauko Tamika masa tana murmushi shima murmushin yakeyi taredakuma mamakin menene aciki??? Tagane abunda yakenufi tace kabuda kaganie mana""" bamusu yabude biza ce tazuwa Dubai Baki sake yake kallonta yace biza naganie??? Tamurmusa ah takuce "" tanisa tana kallon khadija tace wannan itace kyautar taya murnar auren Ku nabarku kumore amarcinku har Kanwata tasamu rabo""" dasauri khadija tasun kuyarda kanta kasa saboda kunya Usman yarasama dawadanne irin haruffa zaiyi amfani domin yagodemata dakyar ya iyah hadiye yawun bakinsa dasuka kafe yatttaro sauran maganarda ke bakinsa yace Maman Abdul wai dagaske kike kuwa??? Tagyada kanta sosaima aikasan inason farincikinka fiye da nawa inaso kasamu cikar burinkane bazanso kacigaba tatauyewa kanka hakkiba Nalurah kanwar tawa bazata saki jiki dakaiba saboda tanada kunya shiyasa nashirya maku tafiyar kozatadan sake dakai Yasaki lallausan murmushi Alhamdulillah amman naji dadi sosai bansan dawadanne irin kalamai zanyi amfanie wajen godemakina tnx matata Murmushi tasaki najindadi tace basaika godemunba wannan aikinane nashirya maka kayanka""" sauran nata tashirya dan jirgin shadaya zakubi Yayi murmushi yana kallon khadija takasan ido wacce haryanzu idanuwanta suna kasa kosaudaya bata dagoba"" labila kam tashiga tashin hankali dankuwa tana tunanin wannan abun kamar wata munakisar lubabatu tashirya Amman babu yanda zatayi tawargaza tafiyar tunda batada bakin fadin komai akan mahaifiyarta Amman alal hakika ranta baikwanta da wannan tafiyarba Dolene tasamu malaminsu saboda ayiwa khadija saukar qur Anie murmushi tayi afili sanin tasamo mafita lubabatu tana jefar labila da murmushi itama haka kowannensu shikadai yasan ma anar murmushin nasa Labila tace sahiba tashi muje intayaki hada kayanki dankinsan dasafe bazaki samu damar hadawaba tayi maganar tanajan hannunta Tamike jiki bakwari tabi labila kamar rakumie da akala sukuma suka rakasu da idanuwa lubabatu tanayiwa Khadija kallon kingama yawo yarinya tunda kika auri mijina Usman kuwa yanayimata kallon soda kauna yanarayawa aransa zaihuta sosai da Deejarh nsa" saida suka bacewa ganinsu sannan Usman yamike yaja hannun lubabatu suka dawo falon saman kujera suka zube Yakuramata ido yana murmushi itama shitakeyi tace yadai mijina""" yamuskuta lubcy wlh mamaki kikebani sosai"" tarausayarda kai tace mamakin menene??? Yace yanda kike kyautatamun wai anyama zamanin nan za asamu mata masu irin halayyarki??? Gaskiya baza asamuba""" tace nidai kadaina fasamun kai da dadin bakin nan naka Yajawota jikinsa yace badadin bakibane wlh dagaske nake nikam nayi sa ar mata tagari wacce kowanne namiji zaiyi mafarkin mallakar irinta""" Hawayene suka sauko akan kumatun lubcy sanyinsu yaji ajikinsa yajuwoda itah dasauri yace lafiya lubcy menene kuma nakuka??? Please banason kukan nan nakie Dan Allah kidaina Tashare hawayenta tace inajin takaiicin kaina daya kasance bana baka hakkinka dayake kaina yanda yakamata inayin hakanne kodan Allah yayafemun hakkinka danaketauyewa ninasan ina cutarda rayuwarka Banason inzama daya dagacikin matanda Allah zaiyi fushidasu Usman yadorah yatsanshi akan labbanta yace bakyacikinsu matata nibaki tauyemun hakkinaba aihakan Allah ya halicceki kuma kinayin iya kokarinki wajen ganin nasamu kwanciyar hankali nagode maki Allah yabarmu tare yasake janta jikinsa yana aikamata wani sako mai rikitarwa Al amarinsu labila kuwa suna hawa bangaren khadija tasheka dagudu saman gado taboye fuskarta""" labila mezatayi inba dariyaba saida tayi mai isarta tace wlh nifa mamaki kikeban kowaya fadamaki yanzun anajin kunyar soyewa danamiji Kinganni nan wlh idan nai aure saina baki mamaki Dan wlh agaban kowayema zannunawa mijina soyayya gashidai kin girmeni Amman ninafiki sanin yanda ake tarairayar miji Tazauna kusa da itah sahiba wannan tafiyarda zakuyi wata damace agareki daxaki saye zuciyar mijinki ki ajiye kunyar nan taki kinunawa mijinki tamkar dagake saishi kuke acikin duniyarku Idan kinataredashi kimanta dakowa kigamsarda mijinki Dari bisa Dari kedin tashice kuma mallakarsa tarage murya kuma wlh karyanemi kibashi hakkinsa kiyita gudunsa Khadija tamike takaimata duka tace waike yaushe kikazama marar kunya bansaniba??? Labila tace ke yarinya zauna nan ainadade inacemaki kifara chating kozaki koyi yanda ake ririta miji kinki hmmm wlh jinake damanice ke danatsula tsiya sai nasakawa wata hawanjinie😕😂 Khadija tatureta tace Allah yashiryaki mom din??? Tace au sorry namanta ashefa mom ce baridai inhadamaki kayan dannasan halinki innabiye maki manyan kaya zakidauka duka tayi maganar tana mikewa tabude drawer tajawo akwatin kayan khadija Tahau duba kayan ciki kananun kaya tayita shiryawa khadija saboda Usman yasiyamata kananun kaya masu masifar kyau Mini sket da kananun kaya gasunan kamar kazanta""" manyan kaya kala uku kawai tasakamata"" takoma hadamata kayan kwalliya komai saida tasaka tace sauran kuma idan kinje karkiyi kwalliyar""" nasan halinki"" danzankirah inji waima ina wayarki??? Khadija tace nafadawa dad fa yakarbomun gida namanta ta wlh kuma inason yin magana da Yayana Amman nakasa tambayarsa koya karbo kumashi baicemun komaiba"" labila tace kinsone wlh dakinason wayadashi aidasaikice inbaki Aron wayata saiki kirashi"" Tamere baki inna hardace nomber din kokuma inbar hardaceba"" labila tace kumafa hakane Amman aidason ranki lanbarda batawuce ashirinba keda kikeda kwakwalwa maikyau kikasa hardacewa Tace kwakwalwata ta karatuce bawai danna hardace tarkacen numbers ba""" labila tace hakanefa ustaziyya Amman kinsan hardace number yanada amfani kodan watarana Bawai ina fataba kisamu kanki inda kike neman agaji abaki Aron waya baki hardace number kowaba yakenan gashima dai yanzu karamin misali kinason waya da ya muktar Amman bakisan number saba Khadija tace kinada gaskiya zanyi kokarin hardace tamutum biyu"" labila tace Yayana dakuma daddy ko ??? Murmushi khadija tayi labila tace bakomai mukoda ba a hardace tamuba badamuwa Amman inafatardai abunda nafadamaki dazun kinkwasheshi afaifan kanki wlh sahiba inajimaki tsoron wata baturiya takwace makishi Aikuwa khadija tahade rai labila tahauyi mata dariya tatashi tabita sukahau zagayen dakin karshedai labila tafada saman gado tana hakiii tace tubanake small momy🤗 Khadija tace aisaikinsha rankashi aka"" labila tarumtse ido takankance kai tanadafe dakai tanajiran saukar rankwashi khadija tahauyi mata dariya tazube saman gadon tace waike atunaninki rankwashinki zanyi aka??? Ainibazan rankwashi kainaba idan dady yasamu baturiya aibanice zanyi kishiba kece dannasan kinfison farincikine fiyedani Kaina yanda kika damu dani nibandamu dakaina hakanba """ Labila tace aisaboda kinsan hakan shiyasa kikemun abunda kikaga dama takwanto saman kafafuwan khadija tace wlh sahiba jinakeyi kamar aduniya bazanso kowa sama dakeba Idan akacire Allah da manzonsa da sahabai dakuma ahalal baitiii idan za akuma tambayana wanakeso bayansu kinsan wazanfada??? Khadija tagirgiza kai labila tace wlh sahiba sunanki zankirah !! Jinake tamkar sabodake akayini kullum soyayayrki sake shiga rainatake bansan daliliba kodan kinason babanane Khadija tayi murmushi tace dama haka Allah yake ikonsa soyayya gamon jinice""labilata tashi zaune takurawa. Khadija ido kamar mainazarin wani abun saikuma tafashe dakuka data tunoda kudirin lubabatu akan Khadija Itama batasan sanda tafara kukanba suka hade kai sunata kuka akarasa Wanda zai rarrashi wanie Aisha✍🏼 ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠ Chapter 85 By Gentle Lady💃🏽 Saida sukai mai isarsu sukadawo rarrashin juna""" labila tace zanyi kewarki sosai sahiba idan kikatafi khadija tace nima haka wlh sahiba Amman karkidamu ga wayanan ai zamudinga waya kodata daddy ce Nibandama wani Abu mezaihana kicewa daddy kema zaki wlh zanfi sakewa idan inaganinki"" labila tace naki wayon aiko nan gani nane yasaka kika sakankance gobe aurenki sati dayafa Amman bakitaba zuwa wajen mijinkiba saikace haka akacemaki anayin auren"" wlh kebandah wani Abu dasaina hadaki da inna airanarda za akawoki bahaka akace kiyiba Khadija ta marairaice fuska kamar zatayi kuka tace daddy nefa yace inbari yafadamaki kizo kirika tayani kwana kokuma haka kurum baikiraniba nidadi miji sai inkai kaina"" Labila tace ayya sahiba kinada gaskiya aibandauka hakan akayiba koni banbaki goyon baya kiyimasa rawar kafaba dole mudanja ajinmu irin namata aikingane dannafiso yagane akwai banbanci atsakaninku """ mudin bamasu arha bane Khadija tace kedai akeji wai mahaukaci yafada rijiya kinga kitashi muje muyi alwala dare yayifa sosai musamu ko hizifi uku mukaranta"" labila takalli agogon dakin yabuga shabiyu da kwata tace hakafa aiyau babu maganar barci hirar bankwana zamuyi Khadija tace nanfadai wlh saina kwanta kinsan bantabaa shiga jirgiba karnaje nayita kwasar barci ayimun dariya tayi maganar tana mikewa labila tace dariyadai waye zaimaki dariya Wanda ya aikeki bayankuma kowa da abunda yashamasa kai babu ruwan kowa dawanie Khadija tace to suda muje muyi alwalar tana dariya tatashi khadija tafarayin alwala sannan labila sukasoma karatu sai uku saurah suka kwanta Washe gari tunda sukai sallar asuba basu komaba sukahau shirya kayansu harda labila dantacemata itama kano zatawuce dazaran tarakasu Bayan sungama suka gyare dakin "" dasauran inda suka bata"" sukai wanka suka shirya sannan suka fita falon kasa Usman yanakusa da lubcy sai shagwaba takemasa kamar wata karamar yarinya shikuwa saibiyemata yake Haka kurum khadija taji wani iri aranta tayi saurin soke kanta ahankali labila tace kinga yanda akeyi itama data tsufa ballantana keda kike sabon jinie yanzu kike lokacin ganiyarki ta rayuwa Sam Usman baisan dazuwansuba lubcy ce kawai talurah kuma batadaina abunda takeba saima tayi tamkar bata gansuba"" Usman ne yaji kanshin khadija ya yawaita afalon yadago yakallesu dasauri yayi saurin saita kanshi yajanye lubcy daga jikinsa sosai yake jin kunyar labila Khadija tagaidashi bayan sunkaraso ya amsa cikin dakewar murya "" tagaida lubcy itama ta amsa labila tagaidasu sannan suka karasa saman dinner haryanzu Khadija batadago kanta sunyi ido hudu dashiba Tunda suka fara cin abincin yakeson tadago kanta danyakafeta damayun idanuwansa Amman taki dagowa dukda tanaji ajikinta yana kallonta Bayan sun kammala yakirah habu driver labila tafitomata da kayanta sannan takulle bangaren tarike key din"" lubcy ce tafitoda kayan usman driver yakwashe duka yasa mota suka rankaya dukansu Yace banga kindauko mayafinkiba kokina nufin iyah nan zakiyimana rakiya??? tana dariya tace inalaifi aiga yarkunan zata rakaku basainajeba Allah yakai lafiya yace Ameen Takalli khadija tace Amarya asha amarci lafiya khadija tasanne kanta dakansa yabudemata baya"" harzata shiga tadafe kanta"" innalillahi"" wlh nayi mantuwa Usman yace mantuwar me kumata dama haka shirinku yake kosati zakuyi kuna shiryawa karshe saikunje kunmanta wani abun Labila tace kabarta mana tadauko mekika manta??? Tace wlh littafaina da Qur ani kumafa dankar namanta Na ajesu kusa kusa Lubcy tayi karaf tace kekuma banda abunki Kanwata kudazakuje yawon amarci mezakiyi da littafai aikyabaridai harkudawo shima maigidan abashi lokacinsa Labila tace sabodame zatabàrsu dankawai zatayi tafiya sai akace kabar addininka agida kejeki dauko sahiba tamika mata key wlh kar shaidan yarinjayeki ko inakikaje rike ibada saikace dai su oi daba ta dauki addinin dakimaba"" khadija tawuce cikin gidan Lubcy tace aike komai saikin nunawa mutane kinfi kowa """ saikifadàman dawakike??? Labila ta marairaice fuska tace waini meyasa mom batasona daddy yanzufa dawata Yar makarantarmu nake tafashe dakuka Usman yace haba lubabatu yarkiicefa baidace kinamata hakanba"" tace alhaji kanajinfa abunda takefada itah yadace tayihàkà?? Nifa mahaifiyartaçe Yace aibadake takeyiba tafadamaki dawatà Yar skull dinsu take Bandama abinki aikinaji batakirah sunaba koda ma takirah suna tundakedai kinsan bahaka kikeba aishikenan saikibarta""" Tanisa shikenan alhaji yace yauwa kokefa yarnan dai takice komai lalacewarta nibansan dalilinda yasaka bakwason yayan fariba Ainikam hajiya batayimun irin yanda kikemata karfanaje nadawo nasamu kinhanamun ya rawar gaban hantsi"" labila tace aini dad wajen hajiya zankoma saikundawo zandawo Yace shikenan ma dama abdul sai Rigima yakewa hajiya waisaita kawoshi inda kike yauma naso turawa shima adaukoshi yadawo nan Tace idan yadawo dad karatun shifa ??? Daidai kawowar khadija yace kece kikasan hakan Amman wlh danaje kuka Yakama saiya biyoni nakawoshi wajenki"" shibaima tunanin kowa saike Khadija taimasu sallama suka amsa tamikawa labila key din bayan mota sukashiga shikuma dashi da driver suka shiga gaba tana tsaye tana daga masu hannu harsuka wuce sannan tajuya cikin gidan tana sake sake aranta sama tahau taduba inda ake ajemata sako tasamu layar wani murmushi tasaki tana juya layar labila kenan aiduk kame kamenki saina raba Usman da khadija saidai kuma kiyi hakuri Tasheke da wata mahaukaciyar dariya irin wacce *hatsabibin boka* yakeyi saida naja baya dannatsorata nadaukama shine yabayyana agabana"" Tunda suka shiga mota labila saizuba takeyi harsukakai airport sunsamu jirginsu Saura minti talatin yatashi Anan suka zauna zaman jirah duk abunda za ayi akagama lokaci yanayi suka soma shiga jirgi sai lokacin labila tasoma sharar hawaye tana kallonsu harsuka shige tana tsaye saida jirginsu yadaga tanasharar hawaye tana daga masu hannu"" Saida tadaina ganin jirginsu sannan tacewa habu suwuce ganin wani guy yanata kallonta"" tunda sukashiga motar tayi shiru sai sake sake takeyi aranta"" Sunakaiwa gida tace yajirata tashiga gidan lubabatu tana falo tayi sallama tahau sama tadauko jakar kayanta tasauko sannan tace ni mom zantafi Tanisa kigaishesu"" labila tace zasuji hartajuya saita tsaya tace nasan kinturah dad da sahiba Dubai ne akan wani mugun nufin naki kisani Allah yafiku kibarganin bokanki yanacin nasara kidauka komai kika nema aduniya zakisamu awajensa shikanshi damace Allah yabashi domin yayimasa takunkumi kiji tsoron Allah Mom kidaina biyewa wanann bokan tafashe dakuka maitsuma zuciya lubabatu tamere baki Idankundago kai tagado takalli indama labilar take saida tasakecewa please mom badanniba kidaina abunda kikeyi kinemi gafarar Allah Tadago takalleta ahankade tace kingama??? Labila tayi shiru tace totunda kingama nagode da nasiharki muna gaidasu tamike tahaye sama tabar labila tsaye Tabita dakallo saida tabace mata sannan tashare hawayenta tajuya taja akwatin kayanta Tafita"" habu yabude mata tashiga yaja motar akabude masu get sukafita" Fitarsu babu jimawa lubcy taciwo kwalliya tafita itama"" tashiga tanta tsetsiyar motarta akabude mata get tafita tasoma yawo cikin unguwanni kozata samu inda akeyin dahuwar abinci tunsafe har dare abunfa dawahala kuma ance karwani yaganie danhaka badamar tabawa wani kwangila dole dakanta zata binne"" Haka tayita yawo""" duk inda tatambaya daga masuyi dasafe saimasuyin da rana"" kuma tafison ahanya Dan agida tayiyu ba a cika wutar yanda zatayi zafie Su khadija kuwa tunda jirgi yatashi takankame idanunta kamar zatayi kuka sai addua takeyi hakan yasa usman yajawota jikinsa yakwantar harsuka lulaya cikin gajimare"" ahankali tasoma saukarda ajiyar zuciya ba awani dadeba tasoma barci maidadi asaman jikin Usman Dayalurah tayi barci yagyara mata kwanciyarta ajikinsa yarufemata fuskarta danbayaso ana kallonmasa puska tuni shima yasoma saukarda ajiyar zuciya yajingina kansa jikin kujerar jirgin yana tunani Lubabatu tana tsaka dayawo tabaro unguwarsu Danisa indama taje batasan sunan unguwarba bama tataba zuwaba wata yarkasuwace Dan kusa da bakin titi take komai anasiyarwa awajen wata maisuyar doya taganie da dankali da awara Tatsaida motarta tafito zuwa wajenta matar tanaganinta tawashe baki tanamata sannu dazuwa lubcy ta amsa suka gaisa tace nawa doya matar tace hamsin ashirin dankali kuwa goma biyar "" haka awara Lubabatu tace kullum kina fitowa??? Tace tomezaihana hajiya aizama gida banamu bane munada marayu agabanmu Lubcy tace Allah sarki aiyanada kyau kanemi halak dinka kamar dayaushe akesamunki anan??? Matar tace ai hajiya kaman karfe bakwai nake fitowa indorah koko idan yakare zuwa yanzu shabiyu nasoma suyar doya da dankali saidare nake tashi inbarwa yata inkoma gida inyi tuwon dare infito dashi Takwas muke tashi watarana harmunakai Tara"" lubabatu tace kainaji dadi bani doyar ta dubu uku kisa dankali Na dubu daya zandinga aiko driver na yana karbar Mani matar tawashe baki tace kaiii Amman naji dadi hajiya tanata wasar baki tazubawa lubabatu doyar tabata tafiddo kudi sabbi hull Tamika mata sukai sallama takoma motarta hartabar wajen matar tanadaga mata hannu saikallon kudi takeyi tana juyasu bayan lubabatu tayi nisa tatsayarda motar tafito da ledar doya dantasan koda tajeda itah gida bazata iyah cintaba danmaituyar doyarma kyankyaminta takeji tasoma rabon ido kozataga wasu almajirai tanakiran wani Yarugo kamar daga sama tajiii ance banda sadakaaaa aikinki zai lalace dasauri tajuya bayanta bataga kowaba tamiyarda doyar yaron yanazuwa tacemasa wanigida take nema kuma tagane tashiga motarta tawuce daniyar dadare zatadawo ta saka layar Aisha✍🏼 ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠ chapter 86 By Gentle Lady💃🏽 Doyar datasiya da dankali saidai tazubar shara"" tana zauna sai sake sake takeyi aranta"" tamatsu dare yayi""" Su khadija basu suka saukaba sai dayamma"" dama usman yana yawan zuwa Dubai bayazama a hotel gida yake kamawa haryagama zamanda zaiyi Amman gidan kusa dawani babban hotel yake"" mamallakin hotel din shiyakeda gidan yayishine dama saboda saukar baki"" Gidan tsab tsab dashi Dan akwai ma aikatanda suke shareshi su goge kullum saboda irin haka karbako yafado kokuma Wanda zaidauki hayarsa yazamana yanada datti"" Bayan sun aje kayansu saman kujerar falon khadija tazube saboda zaman jirgi Usman haryanzu yakasa gane kanta kumashi yakasa yimata magana Idan tunaninsa gaskiyane Deejarh tana kishinsane"" murmushi yasaki ahankali ganin ko kallon inda yake batayi Rigarsa yacire yabar wando sai farar singlet dinsa"" kusa da itah yazauna yajawo hannunta yace zo injimana Deejarh na wannan cin maganin duk na menene??? Kanta yanakasa haryanzu takasa dagodakai takalleshi"" yanisa please Deejarh na kisaki ranki dan Allah kodai garin nan ne bakyaso??? Kaita girgiza masa alamar ah ah Yace towani abun akaimaki??? Nanma tace ah ah yace shikenan kitashi kiwatsa ruwa nibari insiyo mana abunda zamuci yayi maganar yana mikewa yadauki rigarsa yasaka yafita Tabishi da kallo aranta tace meyasa hakan mezaisa inyi kishi matar sacefa??? Nibataji haushinaba danarikemata miji saini Haba zuciyarta baikamataba mahaifiyar sahibar tawa saurin mikewa tayi tayishirin wanka "" tashiga toilet da addua aljanie haruzzal yana biye da itah saboda cika umurnin shugabansa"" Allahumma inni a uzu bika minal hubusi wal haba isi sannan tashiga take haruzzal yamakance baya koganin gabansa haka yayita bin hanya baiganin komai Khadija kam batasan wainarda ake toyawaba bayan tagama wanka tadauro alwala tanafito wa Usman yana shigowa da sallama ta amsa masa sallamarsa ledarda take hannunsa takarba shima yayi shirin wanka maikawai tashafa sai powder tasaka wasu Riga da siket sundan matseta bakamar siket dinma""tafesa turare tasa hijab Koda yafito hartasoma rankon sallarda take kanta shima yashirya cikin jallabiya yatada sallah bayan sungma sukai addua"" tajuyo da fara a tacemasa inawuni Yasaki murmushi koba komai yaga fara arta yace qalau sarkin zuciya dariya tayi tace nifa dad bafushi nakeyiba kawai yanayin zaman jirginne yasaukarmun da gajiya Yace kedai fadi gaskiya ainalurah dake tungida kiketa shan wannan kamshin harcikin jirgi kinkasa bari muhada ido Ledarda take gefensu yajawo yajata jikinsa yace nasan yunwa kikeji bari kici abinci kozakifi sakewa danni banason ganinki cikin damuwa Sinasir ne damiya dakuma jelof din shinkafa yace wanne kikeso dagaciki??? Dahannu tanuna masa jelof din Yace to inazuwa yatada itah daga jikinsa yaje kitchen din gidan yadauko plate da cup da chokali yazuba jelof din sannan yazuba ruwa dakansa yarika bata abaki tanaci hartakoshi"" Yace ga ferfesun tace nidaikam Alhamdulillah yace tonidai bari naloda yadauki chokalin zaici tarike yakalleta yadaga girah alamar mene??? Tace nima dad zanbaka"" yasaki murmushi tonaji Amman banda katuwar loma kinga bakin yanda yake very small Dariya tayi tanarike baki"" yace yidariyarki an jima nima zanrama"" tadibo abincin tasoma bashi yace wannan saiyawuna suntsinke kafinma tabanie kiyi dasauri kinsanfa cinedani kamar gara Tayi dariya kai dad tobari nadinga baka dasauri tayi maganar tanaciko chokalin harbaka"" yace bafa cewa nayi kidibo Wanda yafi karfin bakin nawaba tace to sannan tarage tabashi baiwani cidayawaba yace yakoshi tace kaifa kace cinedakai Yace aiwanda naci bakici korabinsaba""" murmushi kawai tayi tace shikenan jin ansoma kiraye kirayen magrib yamike bari naje sallah"" bayan yafita itama tayi alwala tayi sallah Usman baidawoba sai bayan isah koda yashigo yasamu hartayi barci saman abar sallah tada itah yayi yace takoma akan gado Takoma takwanta sai lokacin yabude wayarsa yashiga wanka yanafitowa kiran labila yana shigowa yadauka da fara a tayi sallama ya amsa yace nasan tundazu kinyita kirah kikajita kashe Tace wlh kuwa kunkai lafiya??? Yashafo Kansa Wanda yake jike daruwa yace qalau muka sauka aitundazu """ muka sauka mantawa nayi ban bude wayarba""" Tace ayya ina sahiba""" yakai kallonsa wajen khadija wacce tasake juya kwanciya saboda jindadin iskanda yake kadata""" yasaki murmushi yace tayi barci ko atada itah.. Tace no barta tahuta nasan gajiyace kawai gobe kaafada mata nakirah yace shikenan harkinje kano??? Tace ah ganima kusa da hajiya tace tana gaidakai yace kibata mugaisa mana tace to""". Sannan tamika mata"" takarba tareda sallama ya amsa hajiya inawuni tace lafiya qalau babangida"" ya khadijar yace qalau take harma tayi barciii Tace ayya aidole Tasha hanya idan kuntashi kagaisheta "" yace zataji hajiya ina Abdul"" tace Abdul Dan Rigima aidarensa yayi yanacin abinci yayi barci"" Usman yace ainahuta kullum nazo saiyadameni anty labila hajiya tace aibakasaniba dayaganta shareta yayi waiyayi fushi saida tanuna masa sweet sannan yaje wajenta usman yayj dariya yace sarkin rigima ai hajiya kina fama" " tace toyazanyi tunda yanace saini aidole inyita hakuri kafin yasamu sabon jini kuma ni awatsani kwandon shara Labila tasomayimata dariya sundade suna fira sannan yayi masu saida safe yashirya cikin kayan barcinsa masu taushi yahau gadon addua yayi masu sannan yakwanta yajawota jikinsa yakura mata ido kamar maitunanin wani abun daga bisani yasaki murmushi yasunbaceta saman kananun labbanta sannan yajata jikinsa barci maidadi yadaukeshi Lubabatu tanaganin karfe Tara nadare yayi tayi shigar ta kamardai almajirah tahau motarta zuwa kasuwar nesa da kasuwar ta aje motarta tataka dakafa zuwa wajen tayi sa akuwa maidoyar tatashi dadan karenta taje Wanda zata tona koda akwai zafi wajen Babu mutane wajen duk anwatse tawuce kamar tana Neman wani Abu daidai wajen mai doyar ta duke taduba babu mai kallontaa wajen kuma akwai ragowar wuta Tajaye garwasun tayi gina tajefa layar tamiyarda toka tarufe tajawo gawayi maiwuta tazuba tamike"" takarkabe jikinta tawuce saida tayi nisa tatsaya taga kodawani bakowa awajen tasakai takoma wajenda ta aje motarta tashiga tatada mota tawuce gida ranta fariii tasss hankalinta kwance bayan tagama abunda zatayi takwanta"" Makale yake da itah kamar Wanda yaji ance za arabasu cen cikin barcinsa yaji kaamar dakinne yakecida wuta Al amarinda yafaru da khadija. Kenan kusan tare suka farka kowanne yaja gefe sukahau kallon kallo"" Usman yamurza idonsa ahankali yasake kallonta yace waibakida lafiyane??? Tayimasa duban rashin fahimta tace mekaganie dad??? Yace jikinkine yayi zafi rau kamar wutaa hannu tasa tashafo jikinta bataji komaiba tace nima naji zafin Amman banyi tunanin jikina bane"" yace shikenan tashi yayi yasake kara gudun ac sannan yacemata sukwanta Sake kwantawa tayi yasa hannu yajawota daniyar tamatso jikinsa zafin dayaji yanzu tamkar anwatsamasa ruwan tafasasshiyar dalmace hakan khadija ma tajiii Amman dukkaninsu gefe sukah koma suna jefar juna da kallo""" Usman yadade zaune sannan yajuya nesa da itah yakwanta yana mamakin wannan suracin dayakeji yana fesowa jikin khadija haryanzu baidaina jin zafinba dolensa yamike babu shiri yakoma falo Yanafita yajishi wasai yasaukarda ajiyar zuciya yana kwantawa saman kujera barci yayi awongaba dashi Bayan fitarsa khadija tadago tabishi da kallo aranta tana mamakin wannan lamarin barcin ma saiya kauracewa idonta ganin kamar tunani zaidameta tamike tadauro alwala tatada sallah Saida asuba tafita falon daga nesa tatsaya tatadashi sannan tajuya dakin bayan tagama sallah saman abar sallar barci yakwasheta bayan tagama azkar Sauri takeyi danyau tadan makara bata tashi dawuriba"""bayan tagama hada kayan kokon tabawa yarta tace taje tadorah kafin tazo tace to sannan tadau itacen dakomai tawuce Dayake banisa daga gidan zuwa kasuwar tanazuwa tazube kayan tashirya itacen tahurah wutaa"" tadorah dahuwar ruwanda za adama koko"" Usman yana kusa da khadija tanabarciii yakuramata ido yana nazarinta firgigit tatashi daga itah harshi kusan taresuka mike Usman yarasa inda zaisa kansa dasauri yajuyaa yabar dakin Amman baiji sassauciba dole yafita gidan yanatafiya dasauriii Saida yayi tafiya mainisa yadainajin komai ajikinsa bakin wata bishiya yazauna yadafe Kansa yanamaida numfashi Bangaren khadija ma saida Usman yabargidan tadainajin zafiii ajikinta""" natsuwa tana dawomata tasoma furta innalillahi wa inna ilaihir rajiun Harkusan azahar batasake ganin Usman ba"" shikuma yanacen dazaran yatunkaro gidan saiyajie kamar anasake huromasa zafii atakaicedai wani hotel Yakama nesa dagidanda khadija take Harzuwa yanzu bakin Khadija baidaina addua ba""" Al amarin mai doya kuwa tunda yarta tadorah koko hartasiyar Amman badukaba tadorah doya harkusan marece hajiyar jiya batazoba gashiyau tayi dayawa kumayau bakasuwa"" kawai saita saukartà tallen suya tajaye wutaa tadauko wuka tahau Gina kasa Saida tayi Gina maidàñ zurfiii saiga layu sunyi jajirr sunata fesarda wutaa"" aikuwa tacirosu tawatsar tadibo ruwa jikinta yanarawà zaninta kamar zaifadiii tawatsawa layarnan sannan tacewa karamin danta yayiwa layar fitsarii Aisha✍🏼 ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠ Chapter 87 By Gentle Lady💃🏽 Mutane sunfara taruwa sunaganin ikon Allah matar tafashe dakuka tace haba nikam nace tunda naga yauba wani ciniki Nasan nasamu wani dan bakinciki wanda yake hassadata yakaini wajen boka😩 Kaibawa ana bakincikin agakana samu saiwani yayimaka munakisarda karasa komai adawo daya to aniyarku tabiku insha Allah babu abunda zaisameni Wani dayake gefenta yace asabe lafiya??? Tace inafa lafiya malam mudi jiyajiya daga ganin masu mota sunfara hwakawa wajena anamun gosulo shine wani Dan banza irin tsiya yakaini wajen wani matsafiii tanuna masa layar tace tunda nadorah kokon safe naga yaunayi kwantai jikina yayi sanyi dama nasaba tona murhuna kafin nahasa wuta yauma tsautsayine ganin mun makara saina turo "" batula ashedai darabon inga wannan Bakar ranar to Allah yafiku inazaune lafiya daku Ashe akwai wadanda sukejin haushina nibanajin haushin kudinda kowa yakesamu Amman yan wadanda nakesamu inciyarda Yayana sune suka tsolemaku ido"" Mutumen yace kiyi hakuri bani ruwa ruwa tadibomasa yayi addua yawatsawa Layun saiga wani hayaki baki kirin yatashii sama"" nan take sailayun suka kama dawuta asabe tabuga salati tace kaganiko malam mudi wato so akayi talauciii yakashemu dani da yayana saitasake fashewa dakuka"" Saida layun suka kone kurmus tokar tabi iska "" malam mudi yace tayi hakuri komai ya war ware tayita masa godiya tace ainasan kaf kasuwarnan babu Maisona da arziki Saikai"" Allah yabar Kauna nagode yankasuwar sukaita mata jaje tace wlh inakallon kowa duk Wanda baizo yayimun jajeba shine tsohon munafukin"" ina kallace dakowa kai yinin ranardai akarasa gane kan"" asabe kowayayi mata yarmagana waccema batakai takawoba saitahayeshi da masifa Hmmm bakutam bayeni meyasa har asabe tasan dakwai laya akasan madafin doyartaba"" asabe babbar macece kuma yarkasuwa maineman nakanta ammanfa akwai masifa batashiri dakowa idanhar ba sana arta akazo siyaba"" tanada wata Kawa jummala dukkansu mazansu sunmutu sunbarsu da marayun yayansu asabe yayanta shida biyar duk matane dayane kawai namiji karamie Jummala Kuwa yayanta bakwai biyar mata biyu maza dayane mailafiyar dayakuwa bashida lafiya komai sai anyimasa ankwantar atayar sunkullah"" abota da asabe tunsuna yammata harsukai aure dasukafara sana a bayan rasuwar mazajensu shine sukezuwa saran doya wajen wata bayeraba Idan sunsiyar sumiyarmata dakudi Sukarbi wata"" anahaka watarana dataje siyen doya maman cinedu take tambayarta wai ina jummala sati biyu batazo karban doyaba kuma bata kawomata kudintaba Asabe tace jummalar??? Maman chinedu tace itafa tazo saubiyu takarbii doya bakudi gashi Nima inadau kotane Dan Allah kishemata takawomun kudina asabe tace Amman da mamaki nimadayake nadan kwana biyu bamuhadu da itah ba Amman bazatarike maki kudiba haka kurum baridai nabiya gidanta injiko lafiya sukai sallama damai doyar tadauki doya tatari Dan adaidaita tafadamasa unguwarda zaikaitaa Bakin kofar gidan yasauketa tabashi kudinsa sannan tashiga gidan tanakwada sallama yayan jummala sunaganinta sukahau gaisheta dayake gidan ba bakonta bane"" tawuce uwardaka jummala tanaganinta tasaki fara a tace maman batulace yau agidanmu shigomana Ta aje doyarta tashiga dakin suka gaisa takirah yarta zulai tace takawowa mamanta ruwa tace to bayan tadibo ruwan tabata tashaa"" tayi Hamdala tanakallonta tace dagawajen maidoya nake tace satinki biyu bakije daukan doyaba kuma baki kaimata kudintaba meyafaru jummala kinsanfa matarnan abunda takemana babuwanda zaimanashi kiituna bashifa takebamu kuma idanbamuda kudi tasake karamana Nifa aganina kodan uwanka bazaiyimaka hakaba wannan zamanin da akeciki"" jummala tace hakane wlh asabe harkunyar zuwanake wajenta bansan yazance mataba kaddarorine idan sun tunkareka bakada maganie sai abunda Allah yayi Asabe kinsaidai akofar gidana nake tuyar doyar nan wlh kullum saina siyar har ana nema watarana kuwa baifi natashi daguda biyuba saina bawa wani kare dayake zama kusa danie kusan kullum saiyazo idan yakwatanci nakusa tashi Kinsan komai marayunda suke gabana dan Adam sai addua keni asabe naga takaina wai Ashe wannan cinikinda nakeyi wata tahademun yawu Tana bakincikina Allah yarufamun asiri dani dayarana babu Wanda yajini akofar wani gidan ina yarmurya ataimakamun natashi nanemi nakaina Amman kuma anajin haushina Kedai bar mahassada watarana nadorah tallen suyana harnagama wlh asabe ko kuda babu Wanda yazoma kusadani gashi nasoye doya Amman babuwanda yasiya ke ingajarce maki labari karenda nakebaiwa doya koshi bairabo inda nakeba inazaune natasa doya gaba inkalli gabas inkalli yamma inazaune hardare sauro yayita cizona harkarfe goma shadaya dole nakwashe kaya nakoma gida ganin kafa tadauke. Tace kinga wajen nan tanunawa asabe dayatsa tace umm nagani inajinki jummala wlh harkinsa jikina yasaki tace hmm kedai bari wlh nan nadorah bokitin doya nayi zaune inata rusar kuka"" Yayana dasukaga haka suma sukaita kuka akarasa Wanda zai rarrashi wanie asabe doyarma kasa cinta mukai kafin safe ta Lalace dole nawanketa tacire kwan nashanya Nasake komawa wajen maman chinedu nakarbo wata nabata hakuri"nace kudinne basu haduba dazaran nasiyar zanhadomata kudin nakawo mata tadauko doya tabanie Nazo nasake daura talle wlh asabe abunda yafaru jiyan shiyakuma faruwa wannan karonkam banyi kukaba nabawa yarana doyar mukaci muka kwanta washe gari muka karya da itah sauran nashanya Najikunyar komawa wajenta sainayi tunanin kodai sungaji da doyarne nazo nakwashi yan kayana dawadanda nafarayiwa zulai cikon aure najinginar dasu Na auno wake nayi awara ke dai bantsiraba danjarin yabalgace Tsawon satii danaga yunwa tanashirin halakamu dani da yarana shine naje kauyenmu kozansamo hatsi wajen Yayana shine yake tambayata nafadamasa yanda sana ar takini Saiyace yanaganin jiface akaimun Amman inbari yafadawa wani abokinsa malamine illaikuwa anafadamasa yace asirine yana nan tsakiyar inda naketoya doya Jikina yanarawa nace Allah gafarta malam kataimakeni yanda Allah yataimakeka wlh marayune dani yace inkwantarda hankalina Inkoma inyi Gina wajenda nake tuyar doyar komai nasamu indauko inkawomasa yabani wani kyalle yace insako ciiki Ai inadawowa nadau abun Gina nazowajen nagina saikuwa gatarin layu nakwashesu akyallen aibankwanaba asabe nakoma Nakaimasa gabana yakarye asirin yace dagayanzu inzan hurah wuta indinga tonawa kafin nadorah ranar nadawo gida damarece inada sauran doya biyu nadafa nafita garka ai infadamaki har layi akamun Jiya jiya naje nakaimasa sadaka nayi godiya Yayana yabanie kudi dayardar Allah an jima zankaimata kudinta nakarbo doya Nasamu jarima dagayanzu babashi zankarbaba Asabe tace kaicho Allah yashiga tsakaninmu da mahassa jummala tace ameeen Asabe tace Amman yafadamaki wacce taimaki wannan danyen aikin??? Tagirgiza kai baifadaba yacedai inbarta da Allah aishi baya fallasawa domin wacce tamun shakikiyatace dab muke da itah Kuma munakusa dakusa nikuma atunanina nakasa gane kowacece Saidai najabaya keduniya ke duniya duk abunda kakeyi saikasamu Wanda yake hassadarka yanzu kiduba kiganie dabara nakezuwa da anfara zundena anacewa dakarfina nakoma maula Amman kuma banje kofar gidan kowaba natsaya narufawa kaina asiri Allah yarufamun Amman nasamu wata tanason tonamun asiri Aini yanzu mutane tsoro sukebanie"" asabe tace ainima kinsa jikina yayi sanyi kicenima indinga tona murhuna kafin nadorah suyar doya Allah dai yashiga tsakaninmu da mahassada jummala tace Ameen sundade sunafirah sannan asabe tatafi tokunji dalilinta wannan yasa kullum sai tatone murhunta kafin tadorah koko wannan layarda taganie bakin gaskiyarta asirine akaimata"" wannan kenan Bangaren khadija kuwa tunda taga Dare yayi Usman baidawoba tadawo harabar gidan tayi zaune tanata rusar kuka"" Usman yanacen harabar hotel din yakasa zaune yakasa tsaye yinicur amasallaci yayishi gashi dare yayi Dan anyi magrib Amman hankalinsa yanawajen Deejarh Yasan dakyar idanma taci abinci kamardai yanda shidinma baiciba kawai yayanke shawarar komawa yafita yabi hanyar gidan saidai baiji komaiba haryakai kofar gidan yahangota duke dasaurinsa yakasara haryana hadawa dagudu Sam yamanta dazafin da yakeji idan ya tunkareta"" Tanajin motsin mutum tadago dasauri tana ganinsa tafada jikinsa tafashe dakuka maikarfii"" gabadaya usman ya susuce yana tambayarta lafiya Amman khadija kamar cewa yakeyi tasake kukan Daukarta yayi kamar yarbebi yashiga falon gidan da itah"" saman kujerah ya ajeta yadago fuskarta ganin yanda idanuwanta sukayi sutu sutu yanuna alamun tadade tana kukan Usman jiyayi duk yatsani kansa saiyadorah laifin akansa meyasa yatafi yabarta"" murya araunane yace please Deejarh Na kukan nan ya isa haka yayi maganar yanajanta jikinsa yasoma shafar bayanta ahankali alamar rarrashi Shiru tayi tanajinsa Amman bata daina kukaba ahankali yace Dan Allah khadija kiyi shiru wlh harcikinraina nakejin kukan nan nakie Aisha✍🏼 ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠ Chapter 88 By Gentle Lady💃🏽 Shiru tayi saidai tarika jan ajiyar zuciya akai akai""" cikinta yashafo yace Deejarh na kinci abinci??? Cikin dasasshiyar murya tace bazan iyah cin wani Abuba dad bayan katafii kabarni saitasake fashewa dakuka Yace ya salam ya isha Deejarh wlh kukan nan nakie yanakashemun jiki kirjina sai harbawa yakeyi"" tace to inakaje dad kabarni nidaya anan bayankuma kasan bansan kowaba Yasake kankameta tamatukar bashi tausayi yace banje ko inaba Deejarh Na ina masallaci inaimana addua"" kiyi hakuri kinji banason kinamun hasarar hawayen nan nakie masu matukar tsada! Tace nidai kayi mun alkawarin bazaka sake tafiya kabarniba"" yasake kankameta ajikinsa yace nayimaki alkawari Deejarh na bazansake tafiya nabarkiba"" Tace kayi alkawari??? Kaiyagyada ah nayi alkawari sake shigewa jikinsa tayi tace nagode dad"" ahankali yasoma Shafa kanta yace gashi anfara kirah barinaje sallah dagacen zansamo maki abunda zakici Tagado dagajikinsa tace kaikumafa??? Idanunsa yalumshe yace nima zanci idan mai sanyi ta taci!" Murmushi khadija tayi tana lankwasa yatsunta nahannu tace shikenan Yamike yadauro alwala haryanzu tana nan inda yabarta yace kitashi kiyi sallar tace to haryakai bakin kofa tace dad tsayawa yayi yajuyo yace yadai mai sanyita"" tace Dan Allah karkadade kadawo gareni🙊 Hannu tasaka tatoshe bakinta Dan itah kanta batasan sanda maganar tafito bakintaba"" murmushi yasakar mata lallausa yace angama deejarh na"" sainadawo yasakai yawuce Khadija daki takoma dafada saman gado tana dariyar kanta gaskiya yakamata tacire kunya tanunawa mijinta tana sonshi kamar yanda yakesonta Tunranarda tadorah ido akanshi taji kirjinta yanabugawa kullum cikin mafarkinsa take tomeyasa itakuma yanzun takasa nunamasa. Itadin tasace Tashi tayi tarungume filo tana juyashi ahankali idanuwanta alumshe tace anya zan iyah zaicefa nayimasa rashin Kunya cikintane ya bada kuuuuuuuu alamar yunwa yakeji saiyanzu tashafo cikinta Wanda yasake lafewa damaya lafiyar kurah ballana antabota Damacikin kamar marar tuwo yake saigashi Kuma yanajin yunwa saiyasake matsewa Murmushi tasaki sannan tamike tayo alwala tatada sallah " bayan ta gama tasoma addu o inta kamardai yanda ta saba"tanaxaune saman abar sallar Usman yadawo da sallama fuskar nan tashi wasai sai murmushi yakeyi"" ta amsa masa sallamar kanta yana kasa kayan hannunsa ya aje yafita zuwa kitchen yadauko plate da cup dawani katon tire Yadawo kusa da itah yazaune yatankashe kafafunsa yajawo daya ledar ya xube kajinda suke ciki manyan kajine anyimasu gashin injin sunsha albasa dakayan yajie saikamshi yake tashi Ya yimasu pillah pillah sannan yacemata bisimillah""" ganin tanadan noke noke kumashi yasan yunwa takeji yace inazuwa Wasu kopunan yadauko yazubamata tea zace tafara dashi danhanjinta su saki babu musu takarba tasha kuma taji dadin tea din bayan tashanye yasoma bata naman tanaci ahankali saida yatabbatar takoshi yabata lemu tasha sannan shima yasomacin ragowar Kuru tayi tana kallonsa daya dagokai saisuhada ido susakarwa juna murmushi"" haryagama""" takwashe kayan"" yace tasamu tayi wanka tadauro alwala shima zaishiga dayan dakin "" kayansa yadauka yakoma dakinda yake kusada nata shimadai ciki da falone da toilet kayan ciki kawaine suka banbanta"" kayansa yacire danshikanshi kyankyamin jikinsa yake tunsafe hardare jikinsa baigaruwaba saina alwala Yadade yana wanke jikinsa kamar Wanda yakeson sauya fata"" sannan yadauro alwala yafito yasharce sumar kansa" yagoge ruwan jikinsa"" maiyashafa wani maisanyin dadi yasaka kayan barcinsa masu kauri da taushi kaman auduga"""yafeshe jikinsa da turare sannan yafita yasameta zaune tana jiranshi"" abar sallar yagyara yashiga gaba yace tataso suyi sallah Bayansa tatsaya yatada sallah raka o"i biyu sukai kamardai yanda akeyi bayan sungama yadafa kanta yayi addu a sannan yasoma tambayarta akan wankan tsarki duk dayasan tasanie haka tayimasa bayanie dalla dallah duk tambayarda yayimata tabashi amsarta daganan yamike yaja hannunta suka koma saman gadon suka zauna hijab din jikinta yacire yace Deejarh abarsaka wannan abun idan inakusa please Batacemasa komaiba yana kallonta. Yace wai bakizoda kayan barcibane?? Muryanta tanadan rawa tace banice nahada kayanba sahibace" baice komaiba yamike yajawo akwatin Wanda haryanzu ba ashirya kayanda suke cikinsaba jerin kayan barci daban yakasosu duka yanadubawa khadija tana kallo duk wacce yadaga saita waro idonta saboda kaf rigunan barcinda labila tasako babu ta mutunci injifa khadija saida yagama ganin kayan duka sannan yadauko mata wata Riga "" rigar milk ce maiturii hade take da bes saidan karamin pant dinta Aituni khadija tahade wasu yawu saida yamiyarda kayan duka sannan yabata yace tasaka tsuru tayi kanta yanakasa"" shidimma itah yake kallo"" Zaiyi magana tace kunya nakeji dad toka rufe idonka" murmushi yasaki aransa yace inada aiki kuwa yajuya yafita falo Yakoma yazauna akan kujerah Kayanjikinta tacire tasakasu"" wata kunya takamata tamatse jikinta dahannunta tace wannan kayan kunyar ina zankaishi tararumo hijab tasaka Tana nan tsaye bakin madubin Usman yashigo yarufe kofa tsayinsa yayi yajingina kansa jikin kofar yarungume hannuwa yana kallonta Ahankali tadago danganin shirun yayi yawa""" sukai ido hudu yace wannan hijabin kumafa banacemaki kidaina sakashi idan muna tareba Gabadaya jikin khadija yamutu bayanda ta iyah idonta yanarufe tajaye hijab din daga jikinta""" masha Allah kalmarda Tafara fitowa bakin Usman kenan Ido yakuramata kamar maisabuwar makanta"" saiyaji bakon al amari atattare dashi Wanda baitabajin irinshiba ahankali yatako zuwa inda take kirjinta yanasake harbawa saboda tsoro Fuskarta yatallafo da hannunsa yana kallonta da idanuwansa dasuka soma rikida daga farare zuwa ja yasoma shakar kamshin jikinta jikinsa harrawa yakeyi dagashi har khadija kafafuwansu kasa daukarsu sukayi Sukazube kasa wannan cedamarda Usman yasamu yasoma sunbatartà"kirjinsa yana harbawa dasauri khadija kuka tasomayi ahankalie Yatsaya da abunda yakeyi yana kallonta murya dausashe yace Deejarh kitaimakeni wlh zan iyah mutuwa idanhar bankusa"" bakinsa tarufe dahannunta tabude idanunta dasuke tsiyayarda hawaye daga gefe tace dad karka roki abunda yake mallakinka Nibazan hanakaba kadakuma kukana yahanaka abunda kayiniya""" gashin kanta yashafa yace zan iyah hakurah inkauda kai dasauraren komai Amman banda kukanki Tadanyi murmushi Duk da a tsorace take Amman babu yanda zatayi halak dinsane""" ahankali tajuya kanta gefe tanamai lumshe idonta daukarta yayi yadorah akan gadon sannan yakashe masu hasken dakin Wannan Daren shine nafarkon darenda Usman zairubutashi acikin tarihin rayuwarsa "" Daren yakumshi abubuwa da dama Wanda babu Wanda zaisan sirrin dake cikin Daren face Usman dakuma khadija Tunda Usman yake baitaba tsintar kansa cikin farincikiba sama da na darenyau jimayake tamkar bashidin bane waidama akwai ranarda hawayenda suke sauka akan fuskarsa zasudaina kwaranya Ada mata bugu daya yayi masu Amman yanzu Deejarh nsa takaryata maganar zuciyarsa lallai ko acikin matan kowa dahalinsa Abu maikyau shine idan zakayi aure ka auri yargidan mutunci mai ilimin Islam Usman harda kukan farinciki yayi awan nan Daren"" dare sukutun bairuntsaba"" hakazalika Deejarh nsa bata nuna masa gajiyawar taba Karshe dankansa yabarta saboda tausayinda tabashi toilet yashiga wajen wanka yazauna yadarji kukansa kamar mace nidariyama yabanie😂😂😂 Bayan yafito yahadama khadija ruwa shiyataimaka mata tagasa jikinta yanadota a towel yagyara masu gadon sannan yashimfideta" Janta yayi cikin jikinsa yanashafa kanta ahankali saida barci yadauketa sannan yamike yasake dauro alwala yatada sallah domin nuna godiyarsa ga Allah dayabashi wannan tukuicin nahadashi da wacce zata soshi fiye dayanda yakesonta Wacce zata dauki damuwarsa kamar tata ya Allah kabarni tareda Deejarh na ka mallakamun zuciyarta Aisha✍🏼 ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠ Chapter 89 By Gentle Lady💃🏽 Bayan yagama yadaga hannu sama yadinga gwararo godiyarsa ga Allah madaukakin sarki yakirasa da sunayensa tsarkaka zazzabine maikarfi yasaukar masa Saman abar sallar yadankwanta nantake yasoma rawar sanyi bashi kadaiba har khadija tashi yayi dakyar yakashe ac dayake cikin dakin yahau gado yaja bargo yarufesu babu jimawa wani nan nauyan barci yadaukeshi Sai shida saurah yabude idonsa sunyimasa nauyi sosai tamkar banashiba""" dakyar ya iyah tashi zaune yakai dubansa wajenda khadija take yadaga hannunsa ahankali yashafo fuskarta tayi zafi rau dasauri yajaye hannunsa"" ahankali yasoma tashinta ganin harsun makara gashi har angama sallah Itakanta jikinta yayimata nauyi"" yasauko dakyar yaje yadauro alwala haryafito yana dafe da kaiii yana saramasa kamar zaidare gida biyu khadija tana Zaune bakin gadon kafafuwanta akasa Amman takasa takasu "" yalura dahakan shikanshi gayanda yakejin jikinsa haka yatallafota haryakaita toilet din yasaukar da itah yadawo waje yatsaya saida tagama abunda zatayi tabude kofar tanajan kafarta ahankalie Sake daukarta yayi yakaita saman gado yashimfida abar sallah sannan yadauko hijab dinta yasakamata"" yatada sallah bayan sungama sukai addua dayake khadija tahardace azkar datakeyi safe da yamma duk daciyonda takeji baihanata yinsuba Bayan tagama tasake kwanciya saman dardumar barcii mainauyi yasake dauketa" koda Usman yajuyo hartayi barcii yasafo fuskarta cikin tausayawa aidole zazzabi yakamata irin juriyarda tayi jiya duk da karancin shekarunta"" dakyar yamike yasake daukarta yadorata akan dago wayarsa yadauko yakamo lambar wanda yakeda mallakin gidan yafadamashi yanason aturo mashi doctor mace bashida lafiya dashi da iyalinshi yayi masa sannu"" Bayan yakashe wayar yaga miscall din lubabatu kusan ashirin dabiyar yadanja tsakii yacillarda wayar yakoma yakwanta idanuwansa arufe Amman babarci yakeyiba shine kawai yasan abunda yakeji"" Yana nan kwance yasoma jin anayin knock din kofa yatashi dakyar damadai baicire jallabiyarsaba haka yaje yabude kofar gidan"" masu aikin hotel dinne tareda wata doctor baturiya suka gaisa yawuce gaba tana bayansa harsuka kai dakin Taduba khadija tace bawani Matsala zazzabine kawai Kuma akwai bukatar ayimata Karin ruwa kodan taji karfin jikinta"" yace badamuwa shimadai bayajin dadi ahada dashi Kudi yabata tasiyo allurai da maganie dakuma ruwanda za akara masu"" anan dakin akajona masu Karin ruwan acikin ruwan tasaka masu allurar barci kodan susake samun natsuwa babu jimawa sukai barci bataje ko inaba tana nan taredasu har ruwan datasaka suka kare khadija aka sake sakawa wasu shidai basai ansake sakamasa wasuba Daya saura yafarfado Alhamdulillah yadanji karfin jikinsa yasamu yawatsa ruwa ma Sudan zafi yasha tea yayi sallah sannan yadawo dakinta doctor dintake tareda khadija Tayimasa yajikin yace Alhamdulillah kudi yadibo masu yawa yabata yace tatafi idan ruwan sunkare shizaicire mata"" tace to tayita godiya sannan tatafi Kusa da itah yazauna yazubamata ido bayako kiftawa sai murmushi yakeyi Wanda shikadai yasan ma anar murmushin"" Bayan ruwan sunkare yaciremata alokacin tafarka"" yataimaka mata tawatsa ruwa tayi sallah"" ma aikatan gidan yakirah suka karbomata abinci yabata saida tace takoshi sannan yamiyarda itah kan gadon shimà yakwanta Yadora kanta akan kirjinsa yana Shafa lallausan gashin kantaa ahankali yasoma magana"" Deejarh ahankali ta amsa yace yajikin nakie" ahankali tace naji sauki yanisa Allah yakara saukii tace Ameen Shirune yabiyo baya nayan dakiku sannan yamuskuta yace Deejarh na bansan wadanne irin kalmomi zanyi amfanie dasuba wajen godemaki akan ni imarda kika jiyardanie Daren jiya Sauran kalamanda suka rage abakina bazasu isah ingodemakiba koda zantattaro dukkan dukiyarda namallaka aduniya nabakie nasan basukai Rabin darajar abunda kika mallaka munba "" banida abunda zanbaki Wanda zaizama tukuici aganina komai zanbaki kamar narage darajar abunda kikabanine Babu abunda zaizama tukuicinki anan duniya danbanidashi saidai inroki Allah yayimaki sakayya dagidan aljanna nagode khadija nadade inajiran wannan ranar harnafitarda raii dasamunta Saigashi Allah majirokon bawansa yasadanie dake alokacinda banyi tunaniba"" wasu hawayene sukasoma sauka akan kumatuñsà""" Sunsoma sauka akan goshin khadija wacce itama kukan farinciki take Wanda Batasan lokacin fitarsuba Jin hawayensa yasaka tadago dasauri tanamai goge nata hawayen takalleshi ahankali tafurta meyasa hakan dad?? Tayi maganar tana shafo ragowar hawayen fuskarsa wadanda basu karasa gangarowaba hannunta yarike yana kallon cikin idonta yasakar mata murmushi yace sanyi kikaji da hawayena kozafi??? Ahankali tace sanyi Yasake murmusawa yasaki hannunta yasake kwantarda itah ajikinsa yace wannan kenuna hawayen farincikine danasameki Yasake kiran sunanta akaro nabiyu ta amsa cen kasan makoshi"" yace kifadamun mekikeso arayuwarki inyimaki amatsayin tukuicin soyayyarki agareni""" Hannuwansa tarungume tace kasonie"" !! Shine kawai abunda nake nema agareka"" yace indai wannan ne Deejarh na kinsamu hakan fiye dazatonki wlh Deejarh inaji ajikina tamkar banida wata wacce nataba so faceke "" zancigaba dasonki harkarshen rayuwata Tashi yayi dasauri yana tada itah zaune yahada hannuwansa danata waje daya yace akwai abunda bakisani dangane damijinkiba bazan boyemaki komaiba na kasance namiji mai tsananin yawan bukata wannan dalilinne yasaka nakeson kara aure saidai duk matarda na aurah karshe saita ha inceni Nafiddarai dasamun matarda zata sharemun hawaye saikwatsam Allah yaturomun dake amatsayin hasken rayuwata yasake kankame hannuwanta hawayen idanunsa suka soma sauka dasauri dasauri yace Dan Allah Deejarh karkema kigujeni saboda lalurarda nakeda itah Nasan dole komai Daren dadewa zakigaji da yawan bukatata bazan ga laifinkiba Amman karkiyi nesa danie"" Khadija duk da kunyarda takeji na maganganunsa baihanata dago fuska takalleshiba tace Allah karyataba nunamun ranarda zangaji dabukatarka Aikin ladar zanyiwa gudu??? Danaga ranarda zakaso biyan bukatarka agareni inki wlh nafison inga ranar mutuwata"" bakinta yarufe yace meyasa zakifadi hakan??? Hannunsa tajaye daga bakinta tace saboda inciremaka shakku da kokonto ko zan iyah bijirewa anan gaba Duk lokacinda kake da bukatar nishadantuwa tokazo gareni nikuma zanzama rijiya maibaka ruwa akoda yaushe zanzame tamkar lambu maikumshe da daddadan kamshi dakuma furanni bazan taba gajiya wajen ganin nafaranta rankaba saboda inasonka Tayi maganar tana mai turah fuskarta saman kirjinsa saboda kunya dayan hannunsa yasaka yasoma dagota Amman taki dagowa dariya yasoma yimata"" yace kidago mana inga idonki dahar kika iyah boye kunyarki saibayanda kikagama magana zatadawo Ninafison kunyar nan tatafi har abada dariya takama yimasa yahauyi mata chakulkuli itama tarama garin dariya tazame kasa saisuka fara mulmula akan gadon idan tayi kasa yadawo sama saitayi sama yadawo kasa kowannensu murmushine kwance akan fuskarsa Dakagansu kasan sunacikin farinciki daga wasa akazarce gamai gabadaya""" sundade suna faranta ranjunansu""" Hajiya lubabatu😂 Zaune dawaya ahannunta tunjiya take kiran wayar Usman yaki dagawa tasaka ranta watakil sunbabe yama yarda wayar Amman duk" dahaka batadaina kirah ba Yini sukutum ajima a jima saitasake Kira Amman babu amsa"" wannan karonma wayar tasake kirah alokacin sungama jindadinsu barci maikumshe da dadi ni ima yadaukesu wayar tasoma kara wayar ya lalabo yadanna yakara akunnensa maisanma wayeba kafin tayimagana yace roll number kawai yakashe saita tasake Kira maimakoñ yadàuka saikawai yaja tsaki yakashe wayar gabadaya Yasake rungume khadijarsa"" cen bangaren lubabatu hankalinta yatashi danba muryar Usman tajiba kardai abunda boka yabata yataba lafiyar Usman yayarda wayarsa wanie yatsinta Dan tabbas wannan bamuryar Usman dinta bace! Towaye🤔 Nikam nace komawaye oho😕 Aisha✍🏼 ☠ *HATSABIBIN BOKA!!!*☠ chapter 90 By Gentle Lady💃🏽 Ana kiran la asar yafarka""" yamike yareda addua""ya Murza idonsa sannan yatashi zaune " ahankali yasoma tashin khadija itama tabude idonta tareda addua zaune tatashi jikinta yasakeyi mata tsamie usman yasauka yayi wanka sannan yadauro alwala yashirya cikin wata shadda ruwan antaa mai duhu masallaci yawuce lokacin khadija itama tashiga bandakin tayi wanka tadauro alwala Sam tayi mamakin yanda barcin yadauketa Bayan tafito tasharce ruwan sumarta tagoge jikinta simple makeup tayi tabude kayanta dazatasa tasaki tsaki lallaima labila yanzu kala uku kawai tasakomun manyan kaya suma acikinsu babu maizanie duk siket ne kuma kayan duk sun matseta gashi dad yahanata saka hijab Haka tadauki kala daya tasaka"" tasa hijab tatada sallah"" bayan tagama tatsaya lazumie tana saman abar sallar Usman yadawo""" da sallama yashigo ta amsa sallamarsa "" kusa da itah yazauna yatankwashe kafarsa"" yana fuskantarta murmushine kwance akan fuskarsa Sam baya gajiya da kallon Deejarh""itama martanin murmushin tamiyar masa""" yana kallonta kasa kasa yace wannan kwalliyarfa ni akaiwa itah??? Tarausayarda kai sannan tadaga masa kaicikin jin kunya"" yace to inhakane yakamata acire wannan hijabin babu musu kuwa tacire""" yasoma kallonta yana mai tasbihi dagodiya ga Allah daya zaba mashi Deejarh amatsayin matarsa Hannunsa yasa yajawota jikinsa tayi matashi da kirjinsa shikuma yana wasa da yatsun hannunta ahankali tace dad wai sahiba bata kiraba??? Sai alokacinne ma yatuna kamarfa yakashe wayarsa"" dantsaki yaja yace inatunaninfa haka kuma nakashe wayata Mikewa tayi tadauko wayar tadawo Tamika masa yabude wayar lambar lubabatu yakamo yasoma kiranta kamar akunnenta dasauri tadauka saitaji muryar Usman yana sallama Tasaukarda ajiyar zuciya tace dafatar kana lafiya?? Yakalli khadija wacce itama shiitake kallo yace qalau nake yagidan Tanisa lafiya tunjiyafa naketa Neman wayarka tanashiga Amman akaki dagawa duk hankalina yatashi nadauka kowani abunne yasameka Yalumshe idonsa sannan yabude yace wlh wayar alokacin batakusa Dani hasalima bansan inda nabartaba dazukuma banajin dadi harda Karin ruwa nasha Lubabatu tahau sallal lamie tace kanwatafa?? Yasake kallon khadija yana murmushi yace ai adalilintane komai yafaru"" Wani farincikine ya lullube lubabatu batasan sanda tatashi saman kujerarba tasoma tikar rawa""" tace toyanzu yajikin naka ?? Yace naji sauki sosai Tarausayarda kai Amman dadyn Abdul mezaihana kadawo gida nifa banaso kayi jinya garinda bakada kowa idan kana kusa dani hankalina yafi kwanciya Yajawo khadija jikinsa yace karkidamu kanwarki zata iyah kuladanie sosai "" sauran kadan lubcy tafado akan kujerah adimauce tace wacce kanwar tawa bayankuma"" saurin dafe bakinta tayi jinta na shirin yin katobara Yace Deejarh mana"" kokinada wata bayan itah??? Tuni zufa yasoma yayyafowa ajikin lubabatu jinyace mata" yadai tayi saurin tattaro ragowar natsuwarta tace Bakomai ina kanwar tawa kabata mugaisa haryanzu lubabatu bata gasgata zancenba saida taji muryan khadija tana ratsa dodon kunnenta"" tace mom inawuni lubabatu tasharce zufa tace lafiya qalau yagarin khadija tace alhamdulillah tayi saurin mikamasa wayar Lubabatu tace kakularmun dakanwata barinadan duba Abu awuta kafin Usman yace to tuni lubcy tayanke kiran "" zufanda yake zuba ajikinta har tarara yakeyi tashiga rudanie sosai wannan wacce irin matace da maganie bayakamata??? Dasauri tamike tayi sama saiga ruwa sunazuba takasan zanenta ashewai fitsarine tasaki lokacinda taji muryan khadija""🙄 Dasauri tahau saman ta lalubo madubinta tashafa tareda kiran *hatsabibin boka* babu wani bata lokacii boka yabayyana Jikin lubabatu yanarawa tace nashiga uku boka asirina yakusan tonuwa cikinta harwani kuka yake saboda firgichi tsawa yadakamata yace kinatsu kiyimun bayanie nibanason Dan Adam maisaurin karaya akan abunda yasa agabansa Saurin karayarki tunfarko shiyasa aikinki baiyi tasiribà kisani nibanyarda darashin nasaraba banyarda da faduwaba kullum cingalaba akan aikina shine farko Lubabatu tafashe dakuka tace Dan darajar tsafinka dakagada ga iyayenkà kataimakeni Wlh komenene zankawo kaikoda jinin mutum ne muddin zansamu inkauda wannan annamimiyar yarinyàr wlh zanyii *Hatsabibin boka* yatuntsure da dariya yanamai kyakyatawa daga bisanie yatsuke fuskarsa tamkar gwaggon biri yace kwantarda hankalinki bukatarki zatabiyaa Amman akwai hadari sosai idan harzaki iyah"" tace mezaihana boka ai komai hatsariñshi zanyi inhar" zansamu biyan bukata yasake kecewa dawata hatsabibiyar dàriyà yace kayanki yatsinke abakin kaba Hayyanul zarri yadawo duka bakaken aljanuna sunkasa rabarta ammanshi yanazuwa yace zai iyah Sharadin da zakibi maiwahalar shi wannan aljanin bayashan jinin dabbobi saina bil adama lokacinda yamaki aiki akan samira dabokanta jiñinsu shiyazama làdar aikinsa Koyanzun yayarda yashanye jinin kishiyarki Amman yace kafin nan dole abashi jinin jinjirin jariri Wanda akagama haihuwarsa ko dimin cikin uwarsa baigama fita daga jikinsaba"" Lubabatu tawaro ido tace nashiga uku"" inazan samu wannan jinjirin??? Aranta tayi maganar boka yasake tintsirewa da dariya yace zanbaki wadansu mangwaro guda uku dazaran kinga maiciki wacce kikasan takusa haihuwa saikibata shi kitabbatar taci ko kadanne"" Dazaran taci aikinki yagama bazatafi mintuna gomaba yaron cikinta zaisoma motsi zaice shifa waje yayi saboda mangwaronda yafada cikinta bazaikara mintuna talatin acikinba zaifito Dazaran kan yaron yafito waje hayyanul zairi yana kusa da itah zaizuke jinin jikinsa koda yaron zaifado aduniya bashida rai"" kekuma dazaran kinbata mangwaron saikisan nayie karkuma kisake taganeki danzatayi tunanin mangwaronki shine yayi silar nakudarta"" Yawunei suka tsinke mata"" tace nagode da wannan taimakon yace saikuma sharadi nabiyu aljani hayyanul zairi bazaitaba iyah tunkarar taba muddin tayi azkar datakeyi dasafe nasha fadamaki masu yawan addu a da sallah sunada matukar wahala aiki yakamasu.. Sannan yarki tanacen tana tayata da addua abunda zakiyi kigggauta samun dabararda zakiyi mijinki yadawo Kasar nan idankuma kinajin tsoron karya zargeki dawani Abu kijira nanda wadansu kwanaki dakammu zamu karkatoda rayuwarsa zuwa gida Dazaran yadawo dole dakinki zai sauka"" saboda kwanakinda yayi batareda keba kinunamasa kema kinada bukatarsa Yarki zamu turamata aljani saagakimu Wanda yake hurawa mutane iskan bakinsa take sihirtaccen barci yadaukesu wannan aljanin shine mukai amfani dashi wajen kishiyarki suwaiba yanata sakarmata barcii Zaije kusa da itah dazaran yaji zatayi addua saiya hurah mata sihirtaccen iskan bakinsa take barci zai dauketa yana iyah sakata barci nawata biyar koma abunda yafi hakan Dazaran mijinki yakwana dakinki lokacinda yakezuwa sallar asuba tareda ma aikatan gidan duka karkiyi barci dazaran sunfita kije kofar dakinta kisandai yanda zakiyi kafin tafara adduar kikirata cikin firgita dazaran tafito aljanie hayyanul zairi zaidauketa dakinga hakan kiyi sauri kikoma benen kasa zakiji anbugeki saikifadi bazaki sake sanin komaiba dawannan zaki Kore zargin kowa akanki Shikuwa saiyafita da itah daga kasar gabadaya sannan yatsotse jininta yayarda gawarta"" zamu rubuta takarda mubarta akofar gidan mijinki yana dawowa""bakin gidan zaiga tashin mota saidai tabadeshi dakurah """ dakinta zamusa shaida atakarda zamuce mumuka saceta kuma bazamu dawo da itah ba duk rintsi karkima nuna waikinga mutanen kisandai karyarda zakiyi. Yana kallonta yace Amman bansan mezai iyah faruwa da mijinkiba saidai kekam aikinki yagama Lubabatu tayi shiru Abu biyune yatashi hankalinta jin za asakarwa labila barci saikuma abunda yashafi Usman kuma gashi idan boka yayimagana bazai sauyaba Tacekai mezaisa indami kaina koma nezaifaru yafaru indai burina zaicika anan tayi sallama dabokan dacewar zatajirah harya karkatoda rayuwar Usman zuwagida Sannan Adan sausautawa labila dazaran andauke khadija atasheta daga barcin"" maganar jinin jinjirin Kuwa abarkomai zatayiii yakasance ashirye ranarkuwa *hatsabibin boka* ya aikomata da mangwaron Tundaga ranar lubabatu take ta yawon neman masuciki Amman duk wadanda tasani dagamai wata uku saibiyu harsu khadija sukai watadaya adubai batasamu mafitaba Khadija da Usman kamar zasu hadiye Kansu saboda soyayya yazata itah tazama shi jiyakeyi tamkar yafasa kirjinsa yasakata aciki saboda soyàyya Aisha✍🏼 ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠ Chapter 91 By Gentle Lady💃🏽 Zaune suke cikin falo tayi matashi dacinyarsa yana wasa dagashin kanta waizaiyi mata kitso itakuma sai wash takecewa Harcikin jininsa yakejin yanayinta yakirah sunanta my heart tace na am hubbyna shiru yayi baice komaiba hakan yasa tamirgina tana kallonsa murmushi yakeyi tace au waidama dankawai kasani amsawane kakira sunana Tamurguda baki takoma takwanta dariya yayi yace bakin nan nakie ya iyah tsokana sosai shiyasa idan nasameshi bana ragarmasa Tadafe bakinta tace au ashefa harda mugunta kake hadamun lallai zansan yanda zanyi nasamu Abu maidaci nasaka abakina aidazaran kaji daci zaka cire bakinka Takai karshen maganar tana tashi daga kan kafarsa tana dariya ido yakuramata aransa yace wai itah komai tayi sainaga takara kyau komai kyau yakemata Ganin yakafeta da ido yana murmushi taturo baki kamar zatayi kuka subhanallah wani masifaffen kyau takara datayi hakan""" hannunta yajawo tamatso kusa dashi hancinsu yana gugar juna suna kallon junansu yace koda kinsaka Abu abakinki Inhar zanhada bakina dawadan nan kyawawan labban nakii danyatsansa yasaka yana zagayen karamin bakinta itakuma tanabinsa da kallo yacigaba babu abunda zanji bayan zakie Wanda yafi Zuma dakomai dakika sanie Ya sassauto da muryarsa yace wlh Deejarh dazanwuni inkwana ina tsotsar wannan bazandamu da abinciba saboda dadinsa muah yasunbaci yan yatsunsa kinga Kuwa komai yarabeshi zaizama sweet ne yakanne mata ido daya Kanta takada tace bawanin nan sai idanhar ba dacin kalasaba aikomai da mazauninsa zaki danashi haka daci inamai tabbatar maka idan nashafa shuwaka a bakina hmmm kai ko abincima bana tunanin zakaci aranar tadaga masa girah tana dariya Kuru yayi yana kallonta aransa yace wai idan narasaki yazanyi??? Yayi maganar yana buga uban tagumie Deejarh tatsaya da dariyarta ganin yanayinda yashiga tace meyafaru dad??? Tayi maganar tana jaye hannunsa daga taguminda yayi cikin yanayin damuwa yace wlh inaji ajikina kamar wani bakon al amari zaisameni Yayi shiru daga bisanie yace inarokon Allah yasa komene zaifaru karyabiyo tawajenki banason narasaki idan narasaki wlh zan iya rasa rayuwata gabadaya Jikin khadija yayi sanyi takwantarda muryarta tace haba masoyina annurin zuciyata kasani komai ruwa komai iska komai rintsi inataredakai bazantaba gudunkaba Muddin ina nunfashi adoron kasa bana tunanin akwai wani Abu dazai nisantanie dakai kadaina saka damuwa Aranka Dan Allah Wlh damuwarka daidai take darashin kafiyata nakwana arba in dazaran naganka adamuwa duka natsuwata nakan rasata kaima kasan inasonka indai tawajenane bazaka samu matsalaba tayi maganar tana riko hannunsa Yace nasanda haka Deejarh Na nasan bazaki taba gudunaba Amman tabbass akwai abunda zaifaru Dan gabana yana tsananta bugawa akullum kamar lokacinda zanfara haduwa dake Tuni idanuwanta suka kawo ruwa"" ido yaware yace kesarkin kuka wasafa nake waimakinsan me??? Batace komaiba kuma batadaina kukanba yace tunani kawai nake dazaran munkoma gida duk wannan soyayyarda kike nunamun zakibartaa Harnadawo kalar tausayi yayi maganar yana turo baki kamar yanda takeyi aikuwa tasoma dariya gakuma hawaye sunazuba a isonta Yace umm ansamu mugunta dole ayidariya waishinkam agarinku akeyin wannan??? Tace mefa??? Yace kuka da dariya alokaci daya mana abun mamaki🤔 Tace habadai yace mubar zancen wasa Dan Allah koda munkoma karkirika jaye jikinki danie kinjii"" yamarairaiçe fuska kamar zaiyi kuka Tace toyazanyi kaima kasan inakunyàr mom sannan kuma sahiba haba nidamunkoma zanjaye jikina"" Usman yatsuke fuska yace wannan akekirah taleko takoma"🙁" to idan kikaihaka nikuma menene ribata wlh daredaya zakiji likita yace ciwo yakamani 1 Ciwon rashin jin dimin jikin Deejarh na 2 ciwon rashin tsotsar my sweet 3 ciwon rashin kwanciya taredake 4 ciwon soyayyarta da shakuwarta Ke atakaicedai zaice maki jinina yahau Amman Na soyayya"" namakance Amman narashin ganinki kusadani nazama kurma rashinjin tsiwar nan takie Ke intakaicemaki labari zaice zuciyata tabugaa adalilinki wayyo Usman yazama abun tausayi shiru yayi yana kallonta yanda take murmushi yace haryanzu baki sauya ra ayibane ??? . Tarausayarda kai tace sauyi Sam"🙅🏻" inazankai kayan kunyar??? Yace kizubasu bayan dakinmu mana"" tosaidaifa ayi yanda za ayi ko wlh agabansu inrungumeki insakiji kunta kinga daganan kunyar tafita . Tace uhum tanan zaka bullo tosaina daina fitowa sahiba tarika kaimun abincina dakie"" yace karkimun haka kinji wlh badawasa nake maganarba Tace ainima badawasa nakeba mezaisa naguji mijina bayankuma yazama rayuwata yazama farincikina inhar zan iyah kauracewa numfashinda nake shaka akoda yaushe tozan kauracemaka Kasa aranka duk sanda kakirah Deejarka acikin zuciyarka zatazo dagudu tarungumeka Tabaka kulawa "" shinko kataba sanin akwai wadansu zuciyoyi masu amsa amo taredajuna sukanyi shawara dajunansu hakazalika sukan amsa kiran junansu wadan nan zuciyoyin bawasu bane face zuciyata da taka Dani dakai abudayane tanisa waikana tunanin zan iyah yinnesa dakaine"" kasabamun dajikinka nasaba dakwanciya asaman faffadan kirjinka bansan soyayyaba sai akanka kashayardani giyar sonka Nashata sosai hartana Neman illatani muddin ka kauracemun zan iyah rasa raina saikawai tafasheda kuka tofa wai anadara gadare yayi tuni Usman ya susuce sai sambatu yake saki menene yasaki kuka my heart wlh bazan taba iyah yinnesa dakeba bazantaba kaura cemakiba Dan Allah kidaina yimun hasarar hawayen nan nakie Tashare hawayenta tace nasanda haka kawai ina tausayin kainane danasabarwa zuciya da soyayyarka wacce zata saka nashiga damuwa aduk sanda nawara ido bangankaba!! Shiru tayi usman yagano maganarta toyazaiyi??? Inama khadija ce yafara aurah ba lubabatu ba dahar abada bazaitaba iyah yimata kishiyaba" ahankali yasoma rarrashinta yace koda yaushe kikaso ganina zankasance taredake har acikin barcin kima yayi maganar yana dago fuskarta yasoma kissing din bakinta rayuwa kenan soyayya tanada dadi aure maikumshe da rahama da nishadantuwa""" Allah yasada kowa da masoyinsa na gaskiya dankuwa duk matarda Takai mijinta wajen boka danyasota kodan karyamata kishiya kodan tajuyashi yanda takeso inaso tasani wlh karya take bata sonshi Bawannan ake kirah soyayya ba" abunda ake kirah so kiso duk wani abunda mijinki yakeso farine ko bakine matukar dai abun baisabawa addiniba kuma baisabawa koyarwar *Annabi Muhammad (S A W)* to tazama mai murna dahakan kaitamafi mijin jindadi wannan shine cikakkiyar soyayya Tuni Usman yamantarda khadija bacinran datake ciki idan sunatare kowannensu mantawa yakeyi dakowa sunaji tamkar babu wadansu mutane aduniyarsu Tamkar sune kawai suketa shawagi awata duniyar daban usman yana rikita khadija da zazzafar soyayyar shi " shikanshi baisan ya iyah soyayya irin hakaba saiyanzu Ashedai komai lokacine dashi duk Wanda yake faranta maka bakasanin sanda sonsa da kaunarsa zaiyita linkawa azuciyarka"" Tuni khadija da Usman suka tsallake siradin masoya sunacen sunajin dadin rayuwarsu irinta ma aurata sosai yanzu khadija tasaba dayawan butakar Usman"" dama" cen batadamuwa kuma bata taba nunamasa batasoba kullum tayi sallah tana rokon Allah yasake bata juriya dakuma kokarin biyawa mijinta buktarsa akullum bata mantawa dawannan acikin sujadarta takanyi tsayuwar dare tana rokon Allah karya nuna mata ranarda zata gajie Cikin ikon Allah dakuma hikimarsa khadija Sam batajin gajiya kamarma karamata karfi akeyi Hakika duk abunda kasa Allah aciki baxaka tabeba hakazalika idan kasa abu aranka Inhar na alkhariine sai Allah yataimakeka wajen cika burinka Aisha✍🏼 ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠ Chapter 92 By Gentle Lady💃🏽 Akwana atashi babu wuya khadija da Usman harsunyi wata biyu da sati uku bayan sunyi wata da sati biyu adubai daganan sukaje India sati daya sukawuce America sati biyu dagacen sukawuce kasa maitsarki satinsu daya sukadawo madina sukai sati khadija tayi ziyara tasha kukan farinciki bata taba tunanin zataganta kusa da kabarin fiyayyen halittaba Allah kenan maiyin yanda yaso dagacen suka dawo Dubai suka fara shirin dawowa gida Al amarin sarauniya lubabatu kuwa tunda taga har anyi wata uku harda kwana biyu Usman baidawoba haka zalika duk tayi wayadashi bata taba nunamasa waiyadawo saitace yazauna abunsa yaci amarcinsa Saibayan sungama wayar takama kuka haryanzu ta gagara samun abunda akace takawo ganin wankin hula yanashirin kaita dare kawai tayanke shawarar ziyartar asibiti taje kasuwa tasiyo likaf da safar kafa"" dama tanada manyan riguna ma aikatan gidansu ta aika suka samo mata mangwaro gashi baijima da farawaba "" yana wuya shima dakyar yasamoshi Washe gari tashirya tasaka kayanta Amman batasa nikaf dinba tafita cikin motarta saida takai asibitin tasaka nikaf din taxuba mangwaron da boka yabata ajaka Wanda aka. Dibomata ahannu tatusa raggaduda ajikinta tadawo tamkar maiciki dama tanada sarbano saicikin yataso"" sosai Tafito tana turah ciki tatafi wajen da masu ciki suke zama idan sunzo awo matarda take wajen tafi mace Dari towazataba wakuma zata hanamawa Mata dashegen kwadayi musamman masu ciki dazaran taga Abu saitace yawunta sunkawo tabbas inhar zata fitardashi awajen bashakka duk matanda suke wajen saisunci aikuwa za ayita haihuwa jikinta baiyarda tayi hakanba dankuwa asirinta zaitonu idan hakan tafaru ga mace sama da Dari alokaci daya Tatari layi itace ta Dari da talatin"" zaune tayi waje daya"" tayi shiru matarda take kusa da itah sai zubarda yawu takeyi duk saitaji zuciyarta tana tashi mikewa tayi tabar wajen Takoma cen bayan wani dakin Amman tahanyar masu zuwa awo cen bakin kofar shigowa tahango wata maiciki tafe tanadaga kafarta dakyar"" lubabatu tayi saurin Ciro mangwaronta tanasha Sam batakallon wajenda matar take kamarma batagantaba Hartakawo inda take zatawuce saita dawo tace asslamu alaikum"" lubabatu wacce taturo ciki tace wa alaikumus salam"" Matar tace Dan Allah baiwar Allah inbadamuwa mangwaron kinnan zakidan sammanie yawunane sukadan tsinke"" lubabatu tasaki fara a tace Allah sarki bakomai barinabaki dama biyune aka samomun tasa hannu ajaka tadauko mangwaron tabata"" Matar takarba"" tasoma sha"" tace Amman ba awo kikazoba naga kinzauna anan??? Lubabatu tace shinazo wlh mutane sunyi yawa sainadawo nan din Amman ke aikin makara bakizo dawuriba Tace hmm wlh dakafa nakezuwa kuma akwai nisa daganan zuwa gidanda nake"" lubabatu tace ayya to ina maigidanki matar tace kedai bari tasamu kusa da lubabatu tazauna dakyar tace mijina bayason haihuwa Tunsanda mukai aure Anty saiyana bani wani maganie inasha bansan nahana daukan cikibane sai ranar najishi dadare yanafadawa abokinsa dan nataba samun ciki saida yayi wata uku yazube Ashe lokacinda banda lafiya allurarda akamun tazubarda cikine Nikuma tundaga lokacin sainadaina shan maganin idan yabani saina kaikaici idonsa inwatsar dayalurah nasamu ciki duk da boyemasa danakeyi duk wahalarda cikin yakebanie aikuwa tunda yagano yace waibanida lafiya bariyakirah amun allurah nikam nace fafur lafiyata qalau dayanace saina nunamasa baxan yardaba kuma naji firarsa da abokinsa Tundayago naji yace koda tsiya sai anzubar danshi baiyi shirin tara yaraba nayi kukan takaici da aurensa dama shine illar ka auri Wanda bakasan asalinshiba .. Sanda yazo aurena iyayena basuyi wani bincike akansaba ganin yanada kudi kawai aka auramunshi "" gashi iyayena yan Cameroon ne acen ya auroni"" yakawoni nan banida kowa bansan kowaba"" tundaga lokacin yakwashe kayan abincinsa duka baya bani abinci duk da katon gidan da nakeciki saidai inje inyo bara asace inci abinci idankuma yakamani yace wai Zanzubar masa da mutunci yalakadamun shegen duka Amman banfasa zuwaba saboda bazan zauna yunwa takasheniba tuni yahana kowa shiga gidansama Ganin bazan daina fitaba shine yasiyo garin kwaki kullum idan zaifita saiyabani gwangwani daya darabi hakanan bakomai haka zanjikashi inci"" saiya fara shigowa dayan matansa suna holewa matansa suna sakani dahuwar abinci tanan ne nakesamu inci maikyau watarana wasuma harkudi sukebani danyacemasu nidin Yar aikin gidansace Dana lurah cikina ya isah zuwa awo shine nasoma aiki wani gida aboye inamasu wankakau anabiyana harnatara kudi yanzu inajiran kawai nahaihu natara kudin mota zankoma garinmu Dama date din haihuwata Yakama likita yace dazaran nawuce sati banhaihuba indawo togashi harnakara sati biyu"" Lubabatu taji tausayinta sosai tace natausaya maki gaskiya hannu tasaka cikin jakarta tadibo kudi masu yawa tabata tace idan tasauka lafiya tayi hidimar biki dasu tanata godiya harda kukanta Tatambayi sunanta tace Mariya"lubabatu tace kefa??? Maicikin tace saudatu""cikinta taji yafara motsawa tace Anty Mariya barinaga likitan zansameki Annanko "" lubabatu tace ah tatashi tanaturah ciki tawuce Tana barin wajen lubabatu tamike tafita tashiga motarta tacire likaf tana saukarda ajiyar zuciya tatada motar ta cikin farinciki tawuce gida Al amarin maiciki kuwa tana kaiwa cikin mutane ciwon Mara yataso mata taduke dasuka lurah haihuwace suka dauketa aka Kaita wani dakin akakirah wadansu likitoci kunsan likitoci akwai dagawa kowacce akakirah saita ce akwai abunda zatayi Matarda taje Kiran likitocin harda kukanta"" dakyar tasamu wata kiristan tace sutafi koda sukazo saudatu harta gama fita hayyacinta gakan danda yafito Amman barai dantuni aljanin yazuke jininsa Tanazuwa tajawoshi saigawani yakunno kai koda tasoma jawoshi daransa kafin yafito babu rai ko kuka baiyiba itakuma tuni tasuma aljanin yanaganin haka yabace yana mai murna dawan nan jininda yasamu Matarda takirah likitar tayita kuka tana tsinewa likitocin ba ita kadaiba duk matanda sukewajen laifin likitocin sukaganie aidasunzo dawuri dayaran basu hawalaba harsuka kaida mutuwa Abunda basu saniba kowa bayawuce kwanansa Hakika hakane Amman dangane da wulakancinda likitoci sukeyiwa marasa lafiya bakarya bane barinma likitoci mata wlh masu imani acikinsu kalilanne Kumawai musulmai dankuwa MASudan tausayin zakasamu kiristanne Yar uwa Norse shinbakisan ladarda zaki samuba idan kika taimakawa Yar uwarki tasauka lafiya Karki manta"" biyanki akeyi ga albashi ga ladakuma Abu biyu zakisamu Amman saikuga mace tazo haihuwa wlh wasu har Marin mata sukeyi waisuncika raki tasan bazata iya haihuwaba meyasa tayi aure sanda takejin dadinta damijinta meyasa bata tuna wannan ranarba Kosuhau yimata fada waitadamesu da kuka ninan shaidace akan wulakancin likitoci mata waikina tunanin Allah bazai kamakibane??? Koke aganinki bakomai bane wannan mezaihana idan akakawo marar lafiya kirika kwantarmasa da hankali Dagashi harmai jinyarsa kirika fadamasu magana maidadi saikiga kowa yanasonki kobayan ranki wlh zakisamu kyakkyawan yabo zakuji anacewa Allah sarki ai wlh doctor wance mutuniyar arzikice tayikaza tayi kaza Allah daiyajikantà Amman idankedin mugunyacefa kina tunanin Wanda kikayiwa rashin kyautawa danbaida lafiya idan yaji labarin mutuwarki zainema maki gafarar Allah Bazainemà makiba wlh"" sannan kisani wannan abunda kikai sai anyiwa zuri arki kodakuwa kin mutune acikin yayanda kikabari ko jikoki keharkema bakiwuce hakan tasamekiba tundakema kina rashin lafiya kuma kina haihuwa Rokona agareku likitoci kusan irin yanda zaku kyautata alakardu da majinyatanku"" kodakedin ba likita bace Amman kinasaran zamowa anan gaba saiki sanyanda zaki kyautata alakarki Allah yasa masuhakan zasu gyara wadanda basayi kuma Allah yasake sakamasu imani da tausayin marasa lafiya dankuwa duk Wanda kaga bashida lafiya shikawai yasan abunda yakeji aransa idankayiwa Wanda yake gangar ajali rashin mutunci yazakaji idan akacemaka ai majin yacin nan yamutu Allah yakyauta Saudatu bayan tafarfado akanuna mata gawar yayanta tayi kuka hartagodewa Allah tadangana tasan damacen sudin bamasu tsawon raibane tadauki yaranta koda tafito duk masu ciki sungama awo suntafi tace Allah sarki Anty Mariya watakil tayi nemana bata ganniba kuma gashi bansan unguwarda takeba Datakoma gida mijinta yaga gawar yayan yayita kuka Allah yadauki son yayan yasakamasa azuciyarsa sanadin hakan yakamu daciwon zuciya Itakuma tace yasaketa garinsu zatakoma yayita bata hakuri yace wlh yanzun yanason Yaya Allah yadoramasa son Yayansa dukda basa raye harkasa yaduka yana Neman yafiyarta tokunsan tsakanin mata damiji sai Allah tayafemasa Amman tace saiyaje an aunashi Idan bayada cutar HIV batareda musuba yaje tareda itah ma sukaje aka tabbatar bayada cutar komai sannan sukacigaba dazamansu cikin soda kauna kamar yahadiyeta yakeji""" sai rokon Allah yake Allah yasake bashi kyautar yan biyu Al amarin lubabatu Kuwa tatafi datunanin wannan saudatu din ganin tunanin baida amfani kawai tawatsardashi takama harkokin gabanta Ranar Usman yakirata yace gasunan zasu taso"" tasa akashirya masu abinci na musamman koda suka sauka bayan isha"i taturah habu driver yaje daukarsu Sunyi kyau sunyi kiba Usman harwani sheki yakeyi alamun yaji dadin amarci rayuwarsa tayi kyau tunda lubabatu taganshi wani bakin kishi yataso mata baki sake takebinsu dakallo saiga kuka yakwace mata Shikuma Usman daukarsa kukan murnane dasauri yasake hannun khadija yatafi yarungume matarsa yana saukarda ajiyar xuciya ahankali yasoma shafan bayanta murya cikin kuka tace nayi missing dinka sosai mijina"" cikin zakuwa shima yace nima wlh nayi missing dinki matata kullum cikin tunaninki nake Khadija tuni tasadda kanta kasa wasu hawaye masu zafi suka sauko mata ganin idan tatsaya tacigaba da sauraren ma auratan kukanta zai iyah fitowa hakan yasa taja kafarta dakyar tahau na urarda zata sadata bangarenta tadauko mabudin bangaren tabude tashiga bangaren duk yayi kurah Amman batadamuba tashige dakin saman gadonta tafada tasoma darzar kuka marar dalili😭😭😭😭 Aisha✍🏼 ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠ Chapter 93 By Gentle Lady💃🏽 Ah kuka marar dalili mana tunda batada ikon hanashi kusantar matarsa kamar dai yanda itama matar bazata hanashi zuwa gunda takeba Aranta tace waidama haka akejin kishi??? Lallai najinjinawa mom danamijin kokarinda tayi harta iyah barwa dad ni tabarmana kwanakinta bayankuma tasan abunda zamu aikata abunda tayin nan koni bazan iyah ba gaskiya. Gashi daga zuwanmu harnaji daban"" Allah kasamani hakuri acikin zuciyata indinga kauda kaina akansu"" Usman kuwa Sam baisan khadija tabar gurinba sai liliyar matarsa yakeyi"" sundade tsaye sannan taja hannunsa sai alokacin yaduba baiga khadijaba Aransa Sam baiji dadiba kaitsaye bangarensa suka nufa tahadamasa ruwan wanka koda yafito harta fitomasa dakayan dazaisaka bayan yasaka kayan ya simpida abar sallah yarama sallarda take kansa Bayan yagama lubabatu tace suje yaci abinci tasan yakwaso yunwa tana makale da hannunsa suka sauko kasa haryazauna yamike Takalleshi inakuma zakaje"" murmushi yasakarmata yace badadewa zanyiba zanduba Deejarh nane baijirah jin mezata ceba. Yasakai yawuce Tabishi dakallon takaici kamar tature duka abincin takeji kodayake bakomai aidaga yaune yarinya "" Koda yakarasa dakinta harkurya yashiga yana karkabe kurah tana kwance saman gado tanajin sallamarsa tayi saurin goge hawayenta tatashi zaune ta amsa sallamar tana kirkiro murmushi tace waiharkayi wanka Murmushin shima yake yana jefenta dawani kallo kusa da itah yazauna yajuyo fuskarta tanoke kanta yace hmmn kuka kikayiko??? Tace ah ah banyi kukabafa??? Saiga hawaye sunzubo sharrrrr yalakuto hawayen dadan yatsansa yace wannan shine shaidar bakiyi kukanba"" shiru tayi yace saunawa nake fadamaki hawayen nan naki tsadane dasu meyasa kikeyimun asararsu Cikin dasasshiyar murya tace kayi hakuri bazan sakeba yanzumna nakasa tsaida kukanne"" yace tomezaisa dole saikinyi kuka Ahankali tadago takalleshi da idanuwanta wadanda sukacika da hawaye tace nikaina narasa dalilinda yakesani kuka Abudaya kawai nasani nakanji kukan yazo batareda natarbeshiba takai karshen maganar hawayen suna zubowa. Yajata jikinsa ya isah haka Deejarh Na nafuskanceki insha Allah zankiyaye Tasake lafewa jikinsa tana saukarda ajiyar zuciya bayan wasu lokutta yace tashi inhadamaki ruwa kiyi wanka kingafa ko sallah bakiyiba muje muci abincin nasan cikin nan naki yanajin yunwa Noke kanta tayi tace kaje kawai innagama zansauko kar mom taga kadade"" yace kinga kitashi konadaukeki dakaina naimaki wankan dasauri tamike tace yihakuri towel tadauka tashiga bandaki shikuma saman gadon yadan kwanta yana kallon silin tunaninsa daya yazaiyi da kishin da yalura khadijansa tanadashi akansa Sam bayaso yaganta cikin damuwa kuma hakan bashizaisa yadaina kula matarsaba danma yasamu lubabatun maihakurice"" yana kwance hartafito tashirya doguwar Riga tazura bawata doguwar kwalliya tayiba"" tatada sallah saida tagama sannan yariko hannunta suka sauko . Lubabatu tunda suka Dade ranta yasake bacii" tadawo cikin falon tazauna takunna kallo"" kamshin turaren khadijane yadawo da hankalinta inda suke saurin kawarda kanta tayi"" kusa da itah yazauna yace rankiyadade inafatardai banyi laifiba "" murmushi tasaki tace wanne laifi kuma kaida matarka kamardai amarcin haryanzu bai ishekaba Kunya ce takama Usman yadan Sosa kai yana kallon khadija kasa kasa"" itakuwa idonta yana kasa tunda sukazo wajen"" yace bahaka bane maman Abdul"" tace tomene idan amarcin bai ishekaba ashirye nake danasake sadaukar maku da kwanakina harsaikun gajie Aran Usman yace indai zakibiyemu bazamu taba gajiyaba Amman azahiri murmushi yayi yace ah ah aiwan nan makadai mungode kohakan kikatsaya dolene najinjina maki yariko hannunta muje kibamu abinci nitundaxu hadiyar yawu kawai nake Yaja hannunta suka wuce khadija tabisu abaya kamar kazarda kwai yafashewa aciki"saman dinner suka zauna sune gefe dagefe sunsaka Usman atsakiya"" lubabatu tazuba masu abincin sukasoma ci tanagefe tana kallonsu Khadija kam saiyawo take da tsokali acikin plate takasa cin komai"" Usman ya dibo nasa yanufaci bakinta dashi tadago fuska takalleshi murmushi yasakar mata "" yalumshe idanuwansa yabude alamar taci itama tamiyar masa damartanin murmushinsa takarba Sam tamanta da lubabatu tana wajen Rayuwarsu ta Dubai kawai take tunowa ganin hakan yasa lubabatu mikewa takoma falo tacigaba dakallonta dankarta kalli kayan takaici Amman acendinma takasan ido take satar kallonsu"" yayita bata tanaci itama tadauko tasoma bashi idan tayi masa babbar loma yakasa hadiyewa takamayi masa dariya Sosai sun shagaltu sun mantama dawata lubabatu saida suka koshi yagogemata bakinta sannan yaja hannunta suka koma cikin falon suna zaunawa wayarsa tahau ringing yadauko yaduba yana murmushi yamikawa khadija Ganin ansa Yayana takalleshi saikuma tadauka tareda murmushi"" daya bangaren akace amincin Allah yatabbata agareki Kanwata"" tadaga ido takalli Usman shima itah yake kallo tace taredakai Yayana"" Yace yakike ya gidan Yakuma gajiyar tafiya nasan bakujima dasaukaba da mamaki tace waidama kasan bama NaN??? Yace sosaima aimuna waya da dady tabata fuska kai ya muktar Amman shine kokace abanie mugaisa Yace kwantarda hankalinki ainakusa dawowa abunda yasaka bance abakiba banason shegen surutun nan naki zaki iyah share mijinki kiyitamun zuba damadai konakirah Dan inji lafiyarkine Kuma dad yafadamun qalau kike saime kuma Tarausayarda kai tace Amman duk dahaka banji dadiba saina fadawa sahibata"" yace rufanie kisayani bazan iyah da itah ba "" tahauyimasa dariya sundade sunafirah sannan tabawa Usman suka gaisa bayan sungama wayar tace dad kakiramun sahiba inata zuba ido munyi da itah zamu sameta anan Amman bangantaba Yace gawayar nan ahannunki nantake gaban lubabatu yabada rasss khadija takamo lanbar tayita kirah akace ba network karshe tahakurah dole tabashi wayarsa Yace yadai batashiga tace ah taredajan karamin tsaki"" mikewa tayi tace mom saida safe"" lubabatu tace harzaki kwanta??? Tayi hamma wlh nagajie mom zaman jirgi badadi"" tace shikenan Allah yatashemu lafiya tace Ameen batareda takalli inda Usman yakeba tawuce abunta Yakalli lubabatu yace bari narakata indawo kai kawai tagyada masa yamike yabita abaya"" taresuka shiga Na urarda zata sadasu hawa nahudu Suna kaiwa yasunkuceta zuwa dakin "" saisaman gadon yadireta saman jikinta yakwanta rabinsa yanasaman gadon kallon juna sukeyi ido cikin ido "" daga bisani yahade bakinsu waje daya yana tsotsa ahankali cikin kwarewa Sundade ahakan ganin yanashirin wuce gona da iri tamirgina gefe"" tanamiyarda nunfashi kamar yanda shima yayi idanuwansa harsun soma rikida ahankali yasake mirginowa zaisake hada bakinshi danata tasa gefen hannunta takare Cikin kasalallar murya yace menene haka my heart??? Takwantarda idanunta tace basaina fada makaba kasan yau dole zaka kwana wajen mom ne baidace ka aikata abunda kakeson aikatawaba Katuna yanzun bani kadai bace kaje wajen mom nasan zakasamu abunda kakeso acen itama tanada bukatarka"" tunda tafara maganar yake kallon Dan karamin bakinta hartagama"" yace bazanyi maki komaiba Deejarh kibarni nayi wasa dake"" kafin tabude baki tayi magana haryasake hade bakinsu waje daya"" babu yanda zatayi itama tacigaba damiyar masa da martanie dakyar ya iyah raba jikinsa danata yamike yacemata saida safe batace masa komaiba haryafita tabishi da kallo tareda zartowar hawayenta saman kumatu tashi tayi tarufe kofa"" takoma tazauna tayita darzar kuka harbarci yadauketa Usman yana fita baisamu lubcy falon kasaba kaitsaye dakinsa yawuce yasameta kwance saman makeken gadonsa tayi daidai idanuwanta alumshe tamkar maibarci To dama khadija ta takulomasa sha awa ganin lubabatu kawai saiya kashe wutar dakin"" toilet yashiga yasake watsa ruwa yayi shirin kwanciya yakwanta ranarma sosai lubcy tanuna mashi tayi missing dinsa bayan sungama raya dare barci yadaukesu Da asuba bayan Usman yayi wanka yayi shirin zuwa masallaci lubcy batayarda takoma barciba yanafita dakin khadija yanufa yasamu kofarta akulle yayita bugamata cen cikin barci taji tace natashi"" yasakai yafita yatada sauran ma aikatan gidan suka wuce masallaci Saida lubabatu taji Tsit alamar kowa yawuce sannan tasadado bangaren khadija takwala mata Kira khadija innalilahi wa inna ilaihir rajiun shikenan labila tatafi tabarni khadija tun lokacinda Usman yake tashinta bata tashiba Jin ance labila tatafi tabarmu ahirgice tasauko daga kandagon tabude kofa tace mom meyasamu Sahib""batagama rufe bakintaba kawai taji kamar anshafeta nantake tasulale kasa saikuma yasunkuceta batttt yabace Lubabatu tana ganin hakan tasauka kasa dasauri tanasauka saitaji anbuga kanta dagini nantake tafadi kanta yasoma fitarda jinie Koda akagama sallah Usman yaji gabansa yana faduwa yaubaima tsaya haske yafitowa kawai yataso yana kawowa yahangi mota tabar kofar gidansa atsiyace dasauri yakarasa kofar gidan tareda daidaikun ma aikatan gidan dasuke taredashi dankwalin khadija yafara ganie dasauri yadauka cikin mamaki yana kallon gidan dagudunsa yayi hanyar gidan Habune yaga""Farar takardar kofar gidan yayi saurin dauka yabudeta rubutunda sukejikinta layi dayane darabi mune muka sace matarka kuma kasheta zamuyi karka wahalda kanka wajen nemanta! Usman yanashiga gidan ahirgice yaga lubabatu kwance cikin jinie kawai rayuwarsa tayardar masa Deejarh sa aka dauke take yayanke jiki yafadi daidai shigowarsu habu da sauran ma aikatan gidan bayan habu yasanardasu abunda takardar takumsa Aisha✍🏼 ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠ Chapter 94 By Gentle Lady💃🏽 Dasauri suka karasa inda yake habu ne yacewa muhd taimakamun da ruwa Dan Allah dasaurinsa yadibo ruwan yamika masa ya yayyafawa Usman Amman komotsi baiyiba"" aka yayyafawa lubabatu tana farka takwamtsa ihu nashiga uku zaku kasheni"" habu yace kwantarda hankalin hajiya aimune sai lokacin tabude idonta Idanuwanta tasaukar akan Usman Wanda ko motsi bayaya dashi dagawa duk daya dasauri tamike tayi wajensa tace mesuka masa?? Kufadamun mesuka masa"" Habu yace bakomai muje asiviti muhd ne yadauko mota suka taimaka akasa Usman cikin Mota sai asiviti"" likito wajen biyar suka rufa kansa Amman ko motsi baiyiba"" Take hankalin lubabatu yasake tashi tarasa inama zata sanya ranta taji sanyi karfa aljanun *hatsabibin boka* sun tsotse masa jinie Amman aiba hakan mukai dashiba Ganin harrana tayi daya saura bawani haske kawai habu yakirah hajiya yasanarda itah tace itama tana asiviti labila ce batada lafiya Amman tafarfado yanzun hankalinta atashe tace ayimaza azodashi kano khalifa teaching hospital tanajiransu Zata sanarda doctor dinsa Amman basu fadamata musabbabin abunda yasameshiba""" sunsanarda doctor zasu daukeshi zuwa kano akabasu sallama suka kama hanya har kano Koda suka shiga sunsamu hajiya bakin kofa takasa zama anaganin su akazoda gadon Daukar mara lafiya akaturashi zuwa dakin taimakon gaggawa Duk iya kokarinda zasuyi wajen ganin yafargado abun yafaskara abunda yayi matukar basu mamaki gashidai baya nunfashi Amman zuciyarshi harbawa take dasauri dasauri Al amarin aljanie hayyanul zairi kuwa kwananshi daya dayini daya yana gudu asararin samaniya harzuwa lokacin khadija bata farfado daga doguwar sumarda tayiba sakamakon bangazarta dayayi Baisake sa a guda yana guduba khadija tafarfado ahankali tabude idonta Kalmar dabakinta yasoma ambata kalu innalillahi wa Inna ilaihirrajiun Saiyanzu take tuno abunda yafaru ahankali tasoma kallon wani bakon al amari kamar anagudu da itah acikin iska bakinta ne yasoma Karanto a uzubikalimatil lahi tammat min sharrima halaka"" Aljanie hayyanul zairi baisan Khadija tafarka daga doguwar sumaba radadin da yasomaji akirginsa tamkar ya chachumo wuta ahannunsa sune suka ankarardashi Kafin yayi aune tuni sun lankawo daga sararin samaniya zuwa kasa kafin sukawo tunie khadija iskan dake tashi sama yasake sumarda itah Saurah baifi sa o i susauka kasaba akayi wuffff akatare khadija tafada hannun wata farar mata maicike da kwarjini sannu ahankali tasaukarda itah kasa yayi daidai da farkawar khadija Ganinta awata duniyar daban yasaka tafara jadabaya daga zaune wata iskace mai karfiii sukaga tatunkarosu bayan tagama saukowa saiga aljanie hayyanul zairi yabayyana cikin siffar jemage Wani irin wargajine girmansa zaikai tsayin daki fadinsa ma haka""" faratansa manyane masu dauke damanyan kumbuna Bakinsa dauke yake da zakwazakwan hakorah masu matukar tsinie ko wanne daya tsininshi yakai tsinin mashii kaurinshi kuma kamar kaurin takobie Idanuwansa kadai abun tsorone "" idan yayi huciii wutace take tartso abakinsaa Daganin wannan halittar wani mugun tsoro yakama khadija hantar cikinta takada tunda take ko acikin fina finai bata tabayin arba dawata halitta maigirma dakuma firgitarwa irin wannan ba """ Amman wannan karamar aljannar Datake gabansa kamar bera yatsaya agaban kurah Sam bata tsorata daganinsaba""" wata kururuwa yayi wacce tasaka khadija shedewar kunnnuwanta na dakiku arba in Tsawarsa daidai take da tartsatsin wuta gaba daya dajin kansa saida yasauya launi sakamakon wannan karar yayi girgiza saigashi yasake zama wanie katon basamude""" Kallon kallon sukafarayi da aljannar daga bisanie yabude bakinsa Cikin nuna isah dakuma takama yace yake wannan aljannar kisanie wannan kalacina ne kigaggauta barin wajen nan tunkafin fushina yasauka akanki Cikin murmushi tace kai awa kuma kaiwanene dazanbaka itah"" inabaka shawarar Kayi saurin barin wajen nan tunkafin raina yakaiga bacii Dariya yafashe da itah yace ke kinsan kodawa kike magana??? Tace bandamu dasanin kokai waye bane Amman nasan zaluncine zaka aikata kuma ni naharamta hakan acikin yankina Wata kuru ruwa"" yayi yace yanadakyau yarinya kisan kodawa zakija kafin kifara fada! Nasan kaf duniyar nan babu wani aljaninda baisanda zaman"" jajirtaccen matsafi kuma gawurtacce Wanda yafi kowa sanin sirrukan sihiri wato *hatsabibin boka* wannan dakike ganie aikinsace kuma nine akabaiwa itah jininta amatsayin ladar aikina"" Aljannar tasakeyin murmushi akaro nabiyu tace bandamu dakaiba hakazalika fadar sunan bakin azzalumin shugabanka bazai tayarmun da hankaliba inamai baka shawara ka gaggauta barin wajen nan Aljani hayyanul zairii yayi wani huciii saiga wutaa tayi tartsatsi dasauri wannan aljannar tasa hannu takare dazaran wutar tataba hannunta saikaga tamutu tamkar acikin ruwa take Wannan yasake fusatashi yataso mata kamar zaicinye namanta danye take itama tayi girgiza saigashi tarikida takoma katuwar kada mai tsananin girma dakuma bantsoro Hakoranta manya manya faratanta kamar fartanya kaifinsu da tsininsu yakai kaifin takobiii take itah ma tasoma kururuwa tayi girgiza saisuka fara kallon kallo dagabisani suka rugo dagudu nantake kura tatashi sama bakako ganin gabanka jikake kafff sukahade waje daya karar hadewarsu kaisaikace dutse da dutsene sukahadu Hmmm wai ance fada inba ruwanka dadin kallo zamuga yanda fadan aljanu zaikaya shin ko aljani hayyanul zairi zaiyi nasarar kashe wannan aljanar yatafi da itah??? Kokuwa wannan aljanarce zataci galaba akansa??? Waishinma itah wannan aljannar wacece??? Ya al amarin Usman Wanda yasuma haryanzu bai farfadoba??? Shin labila tafarka daga barcin da aljani saaagakimu yasakata??? Duka amsoshin wadan nan tambayoyin suna cikin cigaban labarin saiku kasance taredanie Kuyi hakuri banda chaji wannan kawai kukasamu Aisha✍🏼 ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠ Chapter 95 By Gentle Lady💃🏽 Tunie Khadija taja baya tana kallon ikon Allah"" sun dade suna murkususu sannan sukasake jabaya kowannensu yana hucii Abun yabawa hayyanul zairi haushi taya wannan tatsitsiyar zata hanashi abunda yayi niya bakaken aljanu ma shakkarsa sukeyi ballantana wannan dabaiwuce yayimata lakuma dayaba"" Bari kawai kafin wankin hula yakaishi dare yanuna mata ruwa ba sa an kwandobane" " aikogaba da gabanta"" take yayi kukan kurah yadauke kadan sama" yasoma wujijjigata"" karshe yawurgar da itah tafada saman wata bushiya take bushiyar takarye saiga aljanar tadawo cikin suffarta tafarko bakinta da hancinta duk yana yoyarda Jini kamar mayanka"" tayi matukar galabaitaa Aljani. Hayyanul zairi ya kyalkyace dawata mugunyar dariya yace bake bace banda abinki mezaikaiki fada dawanda kikasan yafi karfinki??? Tunfarko dakinbani itah cikin lalama dahakan baisamekiba"" bari kiganie agaban idonki zanshanye mata jinie idan ma bakiyi wasaba kema zanhada dake inkashe tunda kikayi kokarin jadanie Yana kai karshen maganar yasake kecewa dawata hatsabibiyar dariya yatasamma gurinda khadija tace tuni khadija tasoma jada baya gabadaya tsoro yahanata yin addua Batasan wanne irin tashin hankali take cikiba Aljanar nan tanadago kai taga bakin aljanin baifi Saurah kamu hudu ya isah wajen khadija ba "" dakyar tabude baki tace ya Allah"" tareda mikewa dakyar tarikede izuwa wani katon basamuden namiji tanarike dawani babban takobi mai matukar tsini dakaifiii cikin guguwa tawuce fuuuuu saigashi ta isah gaban khadija Hayyanul zairi yakalleta da mamaki danbaiyi zaton rauninda yayimataba zatasake tashi kafin yagama mamakinsa muryanta takatsemasa tunani tace kaibakin azzalumi mushuriki kasani Allah bazaitaba baka sa a akainaba bazaka taba shanjinin wannan bil adamarba saboda yafi karfinka Akaro nabiyu inabaka shawarar kagaggauta barin wajen nan idankuma kaki lahira tayi babban bako"" hayyanul zairi ya kyalkyace da dariya jin abunda tafada yana nunata da yatsa yace "" kenan Yar fitsitsiya harkin isah kitsoratani da alamu kingajie da duniyar toyanzu kuwa zanturaki inda ba zaki dawoba take shima yayi girgiza Yakoma wani katon sadauki jikinsa daddaure da kayan yaki kowanne damtsensa daya yakai kaurin cinyar babban mutum Gurayen jikinsama kadai kaganie saika firgita dogone sosai"" tsayinsa zaiyi kamu ashirin tuni wannan aljanar takoma tamkar kiyashe agabansa kwatakwata tsayinta iyah kaurinsa tatsaya Khadija tamatukar firgita daganin yanda yakoma lallai dakyarne idan wannan aljanar zatayi galaba akansa"" wannan aljanar bakinta tabude tasoma hura masa iskaa mai matukar karfiii amman ko gyangyadawa baiyiba"" Takobin dayake hannunta tadaga iyah karfinta tabuga masa akaurinsa"" abun mamaki jitayi yayi kara kamar ajikin dutse tabugashi take takobin yakarye yazube akasaa"" Hayyanul zairi yana tsaye kikam yarike kunkuminsa yana kallonta""" saibayan data gama abunda takeyi""" yadaga kafarsa daya yataketa gabadaya fadin kafarsa bakako ganinta saimotsi take shikuma yacigaba da busar dariyarsa Dakyar tadaga jikinta taciro wata karamar wuka tasoka masa atafin kafarsa taredakiran sunan Allah tuni wukar tahudashi zafinda yajine akasan kafarsa yasa yadaina dariyar dayake yakwalla kara yadage kafarsa wacce takemasa zugi dakyar ya iyah fincike wukar yayar jinin jikinsa yadinga zuba akasa take kasa tasoma zurmawa Duk inda jininsa yadiga yashige cikin kasa saikawai kaga bakin maciji yakunno kai yafito yatasamma wannan aljanar tuni itama tajawo takobinta Tasoma fillemasu kai Amman Abun mamaki duk Wanda tafilleewa kai maimakon yamutu saikuga wasu kawunan sunsake tartsowa ajikinsa Tuni macizan suka kewayeta""" ganin hakan yasa itama tayi kururuwa tatofarda yawunta akasa yinhakan keda wuya saiga wata katuwar mesa tatsago kasa tafito wata irin shirgegiyace """ girmanta zaiyi girman kada babba bakinta yana feshin wutaa Dagama fitowarta kawai tatasamma wadan nan macizan haka tayita lakumarsu tamkar tanacin cinnaku"" ganin haka yasa dai dagacikin macizan tasoma hadiyar yan uwanta tana kara girma saida tahadiyesu duka saigashi tadawo wata katuwar macijiya wacce taruba wannan mesar sau biyu tsayi dakuma fadii takekuma suka soma fada tsakaninsu hayyanul zairi shima saiya tasoma wannan aljanar suka soma fada dazaran yadaga kafa zaitaketa saita goce itakuma takaimasa Sara duk da ko alama bayajin saran"" Sun sake shafe sa o"I biyar suna wannan fadan haryanzu aljani hayyanul zairi baici nasaran sake takar taba"" bakinciki yasake turnukeshi yayi matukar fusata take yakwantsa ihuuu yasoma huro iska tabakinsa tuni iskannan yadauke wannan aljanar dakuma macijiya tareda wannan katuwar mesar yasomayin hajujuwa dasu sama khadija kanta inda Allah yataimaketa tanakusa dawani katon icce Shitakama tarike kam tanata rusar kuka tunda take banda cikin film bata taba ganin bala i irin wannan ba"" kananun bishiyoyi tuni suka soma fincikowa daga kasa sunayin sama komai nadajin yahargitse wannan aljanar tuntanayin kokari dantasauko harta kasa anyi wajen mintuna goma suna shawagi Asama sannan yazubodasu kasa ragafff take wannan mesar dakuma maciji suka mutu ko shurawa basuyiba""" Itakanta wannan aljannar dakyar take iyah daga yatsanta batako ganie daidai "" bayan sa"a guda komai Yakoma daidai sannan aljani hayyanul zairi yatako zuwa gaban aljanar da babban Dan yatsansa yasaka yaturata tamirgina tadawo daidai fuskarta tana kallon sama Yakyalkyace da dariya yasoma yiwa kansa kirari kamar haka"" saini Aljanie hayyanul zairi dangidan kabusa"" fada"dani bala ine mai shirin gaba dagaba Dani saiyashirya "" yaro aikona goye yasan kura saini na *hatsabibin boka* uban hatsabibai duk Wanda yajadakai sunansa matacce asoka kaki mutum mutum yakiga yakwana kiyama"" saini angon mirqiyanatu"" uban sakafilu"" maidakawa maza gunba" faduwar gaba kotsoro badai gareniba da inja baya gayaki kara namutu danni bazan barwa Yayana abun fadaba!" karyarki yarinya bakaken aljanuma sunbuga sunbarni ballantaana ke"" yanagama wannan surutun yajuya wajenda khadija take Tanaganin haka tasake kankame wannan bishiyar tana kuka" girgiza yasakeyi saigashi Yakoma katon jemage mai fukafuki yasaki fiffikensa yasoma tashi daniyar yasunkuce khadija yayi sama da itah Amman kafin yakai gareta saiyaga tabacewa ganinsa wata iskace maikarfii yaji tasha gabansa lokacin yajuya da mamakin inda gawar wannan aljanar take baiga komaiba"" Ashe lokacinda yakoma jemagen nan wannan aljanar ta farfado ganin yakusa dauke khadija saitazama iska tabi ta karkashinsa tasunkuci khadija tabace acikin iskar Saigasu wani katon gidaa maicike dakayan more rayuwa tsakiyar falon aljanar tasauka ahankali ta aje khadija itakuma tafadi gefe tana nisawa dakyar bakinta da hancinta suna zubarda jinie""" khadija kam tun lokacinda wañnan aljanin yasoma tunkarota takankame bishiya tana kuka tasadakar mutuwa zatayi saikawai taji ansureta anyisama saiyanzu tadaji an ajeta kamar asaman kafet sannan tabude idonta Tasoma kallon falon har tasaukarda idonta akan wannan aljanar dasauri takarasa wajenta tadago kanta tadora akan cinyarta tana kuka ganin abunda yasami wacce ta taimaketa Aljanar tasakar mata lallausan murmushi Wanda dadukkan alamu nakarfin haline tabude baki ahankali tace karkiyi kuka Allah yanatare dake babu Wanda zaicutardake Amman rayuwarki tanacikin hatsari Tasoma tari Cikin kuka khadija tace kaina yakulle wlh inane nan??? Meyakawoni nan?? Ina mijina??? Kuma ke wacece??? Waye wannan aljanin dakukai fada dashi??? Kumani menaimasa dayakeson kasheni??? Kifadamun yazanyi nakoma gida?? Wannan aljanar tamurmusa tace babu lokacinda zansamu damar amsamaki tambayoyinki kirike tambayoyinki harnadawo tasakeyin tari yajimin ciwo ajikina dole naje nayijinya kafin raunin yacigaba datafiya ajikina Kizauna nan harnadawo karkisake kifita kofàr gidan nan Aisha✍🏼 ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠ Chapter 96 By Gentle Lady💃🏽 khadija tace ina nibazan zauna ananba"" wajen mijina zantafi " aljanar tasake murmusawa tace kiyi hakuri Amman fita dajin nan agareki babban hatsarine Wannan gidan dakike ganie gidanane kuma shine kawai adokar dajin nan babu wani matsafi ko aljani dazaiganshi ko abunda yake cikinsa Wannan aljanin bazaitaba tafiyaba inhar baisha jininkiba kuma yasan bakibar dajin nanba danyanajin kamshin jininkin Amman bayaganinki""" Muddin kikafita gidan nan kasheki zaiyi danbazai bar dajin nan ba""" duk abunda kikaji karkisake kifita kiduba ko ina agidan nan duk abunda kike nema zakisamu inafatar zaki ji shawarata nabarki cikin amincin Allah tanakaiwa nan tazama hayaki tatashi sama khadija tadaga kai tana kallonta haryanzu data daina kukaba"" harsaida tadaina ganin hayakin taja jikinta kusa dakujerar datake falon tasake barkewa dasabon kuka Al amarin aljani hayyanul zairi kuwa lokacinda yanemi khadija tareda wannan aljanar yarasa sai hankalinsa yatashi yasoma dube dube gashidai yanajin kanshin jininta Amman baya ganinta hakan yasa yasoma sunsunar kasa yanabin saitinda yakejiyo kamshinta yayita tafiya yana sunsune haryadaina jin kamshinta dole yadawo baya indayakejin kamshin nata yaja yatsaya saikuma yafashe dakuka tareda kururuwa aikuwa khadija tamike afirgice Dan kamar agabanta yake haka takeji Tuni tasheka tabude wani dakin tafada ciki kai dakin yahadu iyah haduwa Amman tashin hankalinda khadija take ciki baisa talura da haduwarsaba "" Saman makeken gadonda taganie cikin dakin tafada cikin tsoro""" Dan itah gidan kansa tsoron sa takeyi gatagama yarda dazamansaba "" Aljani hayyanul zairi kuwa yadauke wajen sa o"i goma yana kuka """kukanda yakeyi bawai na wahala bane kukan bakincikine ai abun kunyane agareshi ace wannan karamar aljanar tahanashi Khadija hakan na nuna kenan taci galaba akansa?// dakarfi yace ina wlh karyane ba ataba bashi aiki yakasaba saboda banda yake aljani kuma shima matsafine bayan haka kuma majiyi karfine sadauki yanzu kwatakwata shekaransa Dari biyar aduniya"" kaf aljanunda *hatsabibin boka* yakedasu shine babba bawai agirman shekaruba saboda hazakarsa dakuma kwazonsa babu wani aikinda yake gagararsa duk inda akaturashi babu makawa saiyayi nasaraa dajin Iraqi da *hatsabibin boka* yaturashin yaje yayi fada damugayen namun jeji masucin naman aljanu dakuma bil Adama yakarkashe su yadawo cikin nasara shiyasa *hatsabibin boka* yake jidashi duk cikin dakarun aljanunsa"" Tayama zaikoma wajen shugabansa "" toyace me idan haryafadi ainahin abunda yafaru bashakka girmansa zaifadi kuma zaijawa Yayansa dakuma matarsa abunfada Wanda zaiyita yawo aduniyar aljanu harnabaya susamu abunfadi ga zuri arsa Damadai aikinda akabashi yadauketa kuma yacika aiki jininta ladarr aikinsace yasan duk inda taboye acikin jejin dole tafito kokuma yunwa takasheta gabanza"" Kawai zai zagaye dajin da mugayen tsafaffin namun jeji dazaran tafito sugama da itah shikuma yatsotse jininta yabasu gangar jikinta zaicewa boka yagama aiki yasandai bazaiyi bincike akan hakaba tunda yayarda dashi dawan nan shawarar yayarda"" yayi busaa saiga manyan namun jeji sunata yawo awajen kuraye zakuna damisa bauna giwa "" dadai sauran namun jeji masu firgitarwa Dakuma cutarwa"" sannan yazama iska yatashi sama yabace cikin gajimare"" lokacinda yayi wannan tsapin khadija tasomajin kukan kuraye dana namun jeje hankalinta yasake tashi tasoma kiran sunan Usman tana kuka maimatukar ban tausayi *Kano* Hospital dinda aka kwantarda Usman tareda labila wacce tasoma farfadowa tasake komawa barci likitoci atunaninsu barcin arzikine takeyi Amman basu saniba barcin ciwone domin zaizama cutarwa arayuwarta Yau kwanan Usman biyu kenan dasuma Amman ko alamar farfadowa baiyiba duk wani taimakonda yakamata suyimasa sunyi amman sunkasa nasarar farfado dashi Sun yanke shawarar dayakai gobe baifarfadoba saidai afitardashi waje Lubabatu tunda taga halinda usman yashiga dakuma yarta labila sai hankalinta yakara tashi lallai yazama dole ta nemi boka aibahakan tace ayiba""" Suna zagayeda Usman har hajiya damasu aiki sunyi. zugum zugum lokacinda khadija tasoma kiran sunansa saiga Usman yasoma motsa Dan yatsansa"" kamar anturoshi yatashi dakarfi yace khadeeja!!!! Badai khadeeja na akadaukaba bazai yiyuba hajiyace tafashe dakuka tace badai hauka takamakaba babangida meyasamu khadijar??? Saiyanzu hajiya talurah da waima bada khadija akazoba Habu ne yasheka dagudu yakirah likitoci dakyar aka rirrike Usman ganin yana nema yafi karfinsu yasa akaimasa allurar barcii ahankali yake kiran sunan khadija harbarci yadaukeshi"" hajiya tana share hawaye takalli lubabatu wacce take sharar kwalla tace wai meyasamu khadijar??? lubabatu kam batace komaiba saidai tabita dakallo saida tasake tambaya habu yace suma wlh basu saniba sundawo masallaci kenan sukasamu"" wata bakar jeep tawuce kofar gidan atsiyace koda suka kawo saisukaga alhaji yadauki dankwali saikuma yaruga cikin gidan Nikuma sainaga takarda kasa"" nadauka nakaranta mukayi cikin gidan dasauri saimuka sami alhaji dahajia duk asome bamusan menene musabbabin sumarsaba Hajiya tarabka salati tace tomeyasamuu Khadija??? Hakuri hakuri hakuri wlh banda chajiii fatan alkhairi agareku Aisha✍🏼 ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠ Chapter 97 By Gentle Lady💃🏽 Hajiya tace aibaikamata kutaho dukaba sai asanarwa yan sanda habu yace nayi tunanin hakan kuma ai munbaro maigadi tareda maibawa fulayoyi ruwa da idi maiwankin mota"" duk da bagidan yake kwanaba nasan yanzu yasamu labari Hajiya tace duk dahakan kukoma kusanarwa yan sanda dama anzo dawayar babangidan saina kira abokinsa dpo lubabatu tace suje kawai idan anfadawa yan sandan saita dauko wayarsu dakuma kaya Dan itah ko mayafi batatsaya daukaba Hajiya tace shikenan Amman kidaina kukan nan haka insha Allah zasu samu sauki lubabatu tagyada kai"" da itah da muhd da habu driver suka dawo kaduna Koda sukaje suka sanarwa yan sanda ashema har maidagi yatafi tun ranar yakai report anyi nema har angaji Amman ba agansuba"" anyita sanarwa kafafen yada labarai dagacen gida suka wuce bayan lubabatu tasake jaddada masu asake tsaurara nemanta Bayan sunkai gidan akabude masu get suka shiga"" habu yatsaya magana da ma aikatan gidan "" Tace su habu sujirata tafito kaitsaye tashiga gidan Dasauri tahaye bangarenta tajawo akwatin tadauko madubin tashafa tareda kiran *hatsabibin boka* shafawarta keda wuya saigashi yabayya asaman buzunsa Lubabatu tayi shiru kanta yanakasa takasa cewa komai dominkuwa bataga idon wasaba Dan fuskarnan tashi murtuke take sanadin kuwa wannan karon saboda rudanie ko kayan aikinma bata turoba Jin surun yayi yawà yace idan bakida abuncewa meyasa kika kiramu alhalin muna cikin wani aikin??? Tace tuba nake uban hatsabibai inacikin tashin hankali dakuma rudanie Mijina dakuma yata yaukwanansu biyu basa motsi kuma bahakan mukai dakaiba nidaikawai nace adauke khadija tomezaisa ataba Usman da yata??? Yace maganar yarki yanzun zata farka sauran sihirin barcinne baisaketaba mijinki kuwa dama saida nafadamaki bansan abunda zai iyah faruwaba bayan dauke matarsa Tunfarko kinason mijinki bakyaso kirasashi meyasa kikace akashe kishiyarki??? Tace boka menene alakar kishiyata dakuma mijina Yace soyayya"! Soyayyarda yakemata talinka wacce yayiwa matarsa tafarko danhaka kikaga yashiga wannan halin""" tace to boka mezaihana itah ma acireta dagacikin zuciyarsa"" yace abune maiwahala tamarairaice fuska ataimakamun boka banaso yarika tunawa da ita idankuwa harzaituna da itah kagakuwa babu amfanin kashetan da akayi Kayan aiki daban turoba wlh afirgice nake hankalina yarigada yatashi"" yace karkidamu zanbaki wata laya kisamu kabari sabo wanda akarufe yaudin nan saiki Gina kabarin kisaka layar dazaran kinsaka shikenan koda mijinki yafarka kikaji yana ambatar sunanta karkidamu Danbazai manta da itah lokaci dayaba saidai adadin kwanakinda gawar zatayi cikin kabarin kullum anacire masa itah aransa akwana atashi haryamanta da itah duka wannan itace kawai hanyarda za abi bayanta kuma babuwata hanya yakikaganie Wannan layar dakike gani dazaran kin binneta duk acikinsu har yan uwanta daduk Wanda tasani sannu kan hankali zatafita aransu kamar yanda kikasan idan mutum yamutu lokacinda yamutu anajinsa arai anakwana anarage jin zuzin harma kiga magadan sunsoma mantawa dashi suncigaba da sha aninsu tokamar hakane awajensu tamkar matatta zatazamo tunda damacen bata duniyar saidai wani lokacin zasurika tunawa da itah dankuwa abune maiwahala acireta aransu farat daya Tace abunda kace aihakan za ayi godiya nakeyi boka Kajima kayi karko"" yajinjina kai yace kiduba zakiga layar agaggauta birneta yaudin nan Tace angama boka takeyabace tamiyarda madubin to dama magriba takawojiki har an soma kirah tacewa habu baritaje gidan malam tanemu tasa ayi saukar Qur ani duk indasuke saisundawo da itah yace aihakan yanadakyau Tanafita gida kaitsaye makabarta tanufa tasamu maigadin wajen Suka gaisa tace Dan Allah wani taimako zakamun"" shikam yaga hajiya damota dama yasaba da irinsu Amman saiya tsuke fuska yace wani irin taimako a makabarta??? Dajin hakan sai lubabatu tazuge jaka tadauko daurin kudi yan dubu dubu dubu hamsin tace wannan ne ladar aikinka"" aikuwa yawashe baki yace tome kikeso acikin sassan jikin bil adama"" murmushi tayi tace duk ba wannan ba ankawo sabuwar gawa yau??? Yace dazun nan kuwa aka birne uwani yargidan malam habu "" kai yarinyar akwai"" lubabatu ce tadakatar dashi tace bawai sonake kafadamun halintaba ko dangantakarta da mutane Yace tuba nake tadauko laya tace tsakiyar kabarin nakeson katona kasakamun layar Yace Abu maisauki aikoda nera darima zan iyah yimaki wannan yakarbi layar yashiga tana biye dashi harsuka kai kabarin yatona yasaka layar yamiyar yarufe sannan suka fito tayimasa godiya tashiga motarta tawuce"" Bayan takoma tacewa su habu kawai suwuce bawani bata lokaci suka kama hanyar kano koda suka isa hospital sunsamu inna da malam garba dukkansu sunsamu wannan mummunan labarin Dasukazo ganin labila hajiya take sanardasu ansamu nasara labila tafarfado Amman batacewa uffan tunda su lubabatu suka shiga takurawa lubabatu ido kamar maitunanin wani Abu tuni jikin lubabatu yayi sanyi karfa labila tatona mata asiri kodayake ai anrufemata baki dawan nan tasaki ranta"" andade ana jajantawa juna"" wannan al amarin hajiya tatambayi su habu kosun sanarwa yan sanda sukace ah aikoda sukaje harmaigadi yasanar masu Tace toshikenan "" Allah yasa aganta"" suka amsa da Ameen"" lubabatu tamatsa kusa da labila tace mata yajikin illah kawai tabita da kallo batace komaiba"" Hajiya tace aitunda tafarfado batace kalaba saidai binmu dakallo takeyi oh ni binta wannan Abu duk alokaci daya Allah yabaku ikon cinye wannan jarabawar"" suka amsa da Ameen Saikarfe goma allurarda akaiwa usman tasakeshi tunda yafarka baice uffan ba shima sai tsirarun hawaye dasuke zubomasa akai akai yana sharewa hajiya sai sannu takemasa yanabinsu da kallo Bayan kwana biyu jikinsu yayi dansauki suna amsawa idan anyimasu sannu ganin haryanzu ba labarin khadija su malam garba suka Kira muktar akasanar dashi ranar yataso koda jirginsu yasauka kano Tara nadare kaitsaye yatari dan adaidaita zuwa gida Da sallama yashiga gidan kamar wani mahaukaci yasamu su innah dasu gwaggo hassana sunyi zugun zugun dukawa yayi yagaidasu suka amsa sunyimasa ya hanya yace alhamdulillah Shirune yabiyo baya sannan yace yanzu ina dadyn yake??? Inna tace aitunda yaga dankwalin khadijar baimatsaya jin itah suka daukaba yayanke jiki yafadi yanzu suna asiviti itama labila sai shekaranjiya ta far fado muktar yace nifa abun nan yadauremun kai satar mutum kuma harcikin gidansa ni wlh bana zargin kowa sai Abba danhaka nigobe yola zanje koyabani Kanwata ko wlh inmakashi kotu malam garba yace Dakata dakata bahaka za ayiba taya zakace shikake zargi gadukkan alamu mahaifinku baisanma akwai cikin khadija ba"" kamardai yanda mahaifiyar Ku tace sannan kuma baisan tayi aureba baisan inda takeba haba muktar aiko anan yaci kagane Yayi shiru tokuwa inhakane saidai shi Usman din inyanada abokan gaba lallai dole yaganshi yanadakyau yaje asivitin Yanisa inna to ansanarda yansanda??? Tace ansanardasu"" Amman sunce basukama suba sunanan dai suna bincike yanzu matsalar Usman yasamu lafiya Inna tayi tagumie tace ni wlh tsorona kawai karsu cutarda itah"" wadan nan masu satar mutanen dabasuda imanie tayiyuma kidnapping ne Muktar yace bahaka bane inna Aida kidnapping ne kudi zasu tambaya yanzu wanne hospital din aka kwantarda dadyn"" Malam garba yace ah to yanadakyau kaje danyanajin jiki saidai kabari saida safe mukammu munason sake ganinshi Yace shikenan yamike zuwa bangarenda dakinsu yake zuciyarsa tanayimasa kuna"" Al amarin khadija kuwa tun lokacinda taji kukan namun jije ya yawaita saitaji hankalinta yatashi kwance datake tana kallon agogo tuntana kuka tanakiran sunan Usman hartagaji dankanta tayi shiru Tashi tayi tashiga toilet tasamu akwai ruwa tadibo tayi alwala tazo tayi azahar la asar tadauko Qur'anin dataganie tabude tasoma karatu ahankali taji zuciyarta tanayimata sanyi tana nan zaune hardare gashi babu fitila duhu yafara take tasakejin tsoro Kamar walkiya taga kwayayin lantarki nagidan duk sunkama haske ya mamaye ko ina tamkar rana Saikunyi hakuri yaugashi daya kuka samu wlh yau fitanayi kuma gobe biki zanje zanyidan kokari inyi biyu goben in Allah yayarda I love u all Aisha✍🏼 ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠ Chapter 98 By Gentle Lady💃🏽 Ganin hasken yasaka taji hankalinta yadan kwanta da agogo take amfanie idan lokacin sallah yayi sai wajen karfe dayan dare sannan barci barawo yadauketa Washe gari bayan tayi sallar asuba taji cikinta yana murdawa saboda yunwa tarasa yazatayi inama zatasamu abinci tashi tayi tasoma zagayen gidan dakunanda suke gidan sunkai goma kowanne dakin Kalar kayanda suke cikinsa daban ne danadayan"" karshe tasamu kitchen dakayan ci gasunan kayanmiya gasunan jawur dasu saikuma kayan lambu kawai sutadibo tawanke tadawo falon tazauna tasoma sha takwantarda hankalinta dankuwa tasan baranar zuwanta gida abudaya take tunani Usman tambayoyinda suke cikin ranta sunada yawa kuma tarasa wazai amsamata amsar tambayoyinta Bangaren Usman washe gari muktar yatafi hospital din tareda su malam yagaisa da Usman Wanda kansa yake done baicewa ko wa uffan" su hajiya suka jajantawa juna"" muryan Usman sukaji yace hajiya muje gida haka Dan Allah" Kusan tare suka kalleshi hajiya tace gidakuma babangida aikanabari kasakejin karfin jikinka ko??? Yagirgiza kai hajiya bazan taba warkewaba muddin dagaskene andaukemun Deejarh na inaji ajikina tana gidan nan bakudai duba dakyauba Hajiya tace haba babangida kazama mai tawakkali mana insha Allah khadijarka zatadawo gareka kadaina kukan nan kamar mace tunshekaranjiya haryanzu koruwa baka hadaba aikoyunwa kawai ta isah tasamaka ciwo Murmushi yayi mai ciwo yace abinci hajiya aini nayi bankwana da abinci kamaryanda nayi bankwana da farincikina hajiya nifa bazan ma kwana ananba sainaga khadija Muktar yanisa yace dad kayi hakuri kajirah kasake samun sauki saimuje kaduna gabadaya"" nikaina hankalina bakwance yakeba"" Usman yace wlh tana nan kusadani muktar gashi inaji tanakiran sunana Dan Allah kutashi mutafiii idan bantafiba hankalina sake tashi zaiyi ganindai Usman yakafe lallai sai sunje kaduna babu yanda zasuyi haka suka karbi sallama akarubuta masu magunguna suka kama hanyar kaduna hardasu inna Suna Isowa kofar gidan habu yayi hon maigadi yabudemasu yakunna kan motar motarsu muhd suna baya Dan aciki su muktar sukashigo Anatsayarda motar Usman yafito yayi cikin gidan dasauri kaitsaye hawa nahudu yahaye yabude dakinta anan yacikaroda bargonda ta lullube ahankali yakarashi ahancinsa yashaki kamshinta yalumshe ido jiyake tamkar yanzun khadija tayafashi saboda kamshinda yakeyi"" dakin yasoma dubawa yana kwalamata kirah harcikin toilet yagama bade bagarenta danema Amman baigantaba cikin falon Yakoma yarumgume bargon yafashe dakuka Damadai Usman kuka bayayimasa wuya kamar mace su hajiya suna shigowa basu ganshiba hajiya tace to inakuma yayi lubabatu ce tace yana saman duk tare suka rankaya saman sukasameshi yana kuka Labila takurah masa ido sannan takalli hajiya tace waimeyake faruwane haryanzu banga sahiba ba??? Meyasa dady yake kuka??? dukkansu takebi dakallo tanayimasu tambayar akarasa Wanda zaibata amsa Usman ne yamike kamar Wanda akatsakurah yayi waje hajiya tanakiransa yace policetetion zaitafi muktar ne yabi bayanshi waje sukasamu su habu suka dunguma zuwa opishin yansanda wajen abokinsa idris yatafi dayake DPO ne bayan sungaisa Usman yasanardashi Yace wlh yasamu labari Amman sunanan sunayin iyah bakin kokarinsu kuma insha Allah duk inda take za aganta sundade cen anayiwa Usman tambaya tareda ma aikatan gidan Amman usman yace baya zarginsu dantare sukaje sallah Towama za adorawa laifi haka sukadawo gida jiki sanyaye hajiya tace asanar masallaci domin atashi da addua Allah yabayyanàta duk inda take Lubcy kam dagekawai take kallonsu saiyanzu labila tasan mekefaruwa taci kuka harma yasake jawomata wani zazzabin kullum cikin addua take Allah yabayyana sahibarta yanzukam Sam batadorawa lubcy wannan aikinba Kawai tahakikance akan waninedai maijin haushin babanta"" rayuwa kenan Usman cikin sati biyu karkuso kuga yanda yazama kullum yazauna baidawata magana saita khadija saikuma yawan tunaninta I Kullum zakasameshi bangarenta yatasa kayanta agaba yana kallo watarana yayita surutu saikuma kasameshi yana kuka"" labila makusan hakan saida lubabatu tayita basu baki tuni muktar Yakoma sannu kan hankali labila taware Usman mahakan yasama mata admission tawuce London dantacigaba da karatunta Usman mayakoma bakin aikinsa!" Khadija sannu sannu hartasoma sabawa dagidan abunda yake yawan bata mamaki kullum saitaji kamar anayimata motsi acikinta tun lokacinda tacika wata daya agidan takejin hakan Saikuma yanzun taji motsin ya yawaita gashikuma mararta tasoma tasowa kamardai maiciki yanzun balaifi tanayin hargirki taci kuma dazaran kayan miya sunkare saikawai tasake ganin wasu Bayan watanni uku alokacin kam khadija tasan cikine da itah tashiga tashin hankali ita dabakowa agidan towaye zai taimaka yakaita asiviti gashi bakowa agidan"" koma adadin watannin cikin batasaniba nidai inakan kirgamata watansu uku wajen yawon shakatawa yanzun tayi hudu anan cikinta Yakama kwata bakwai kenan Karkuso kuga kirmansa kamar gobema zata haihu danyagirma sosai duk dayake cikin budurwane!" Usman zaune cikin falonsa suna firah da lubabatu tanacewa yakamata yadauko Abdul majeed yadawo hannunta"! Yakalleta da mamaki yace yanzun kuma kefa kikace bakyason hayaniyar yara Tarausayar dakai tace toyanzun gidan nan yamun fadi nidaya!! Shiru yayi daga bisanie yace shikenan zanyiwa hajiya magana kometace shikenan"" tace harsaika tambayeta haba usman to indai bazaka daukoshiba kasamamun Yar aiki wacce zanrika ganie kuma tana tayanie aiki Yace shikenan kamar dayaushe kikeson ta??? Tace umm Nifa tafiyama zamuyi namanta bansanar dakai ba Usman yakalleta kamar zaiyi magana saikuma yafasa kansa yajingina jikin kujerah yadafe saitin zuciyarsa dayakeyi masa ciwo lubabatu takalleshi tace yadai kociwonne??? Kaiyagyada mata tace sannu yadaga mata hannu alamar yauwa"" tace kai ni wlh ciwon nan naka yasoma isata ayi Abu bayajin maganie Ya murmusa yana lumshe ido yace baisamu ingantaccen maganinda yadace daciwonba"" tace kamar wanne maganie kenan ai atunanina babu maganinda zai gagaremu siyensa komai tsadarsa Yayi saurin tarar nunfashinta yace akwai mana ai maganin ciwona khadija ne muddin baxan gantaba ninasan nayi bankwana da lafiya harkarshen rayuwata Nina San sonta shine zaizama ajalina Ahankali lubabatu taja siririn tsaki wannan abun na Usman yasoma Kaita makurah ko kwanciya sukayi duk ranarda yasamu tabashi hakkinsa babu sunan wacce yake ambata sai khadija Idan yakwanta kwana saidaifa kowa nagidan yadade kunnuwansa dan sunanta yaketa kiran hargarin Allah yawaye abunda yakekuma bata mamaki Sam Usman yanzu baidamu dayakwanta da itah ba Dantun bayan batan khadija yanzu tsayin wata hudu Usman saudaya yakwanta da itah koshi ita tajashi dankuwa haka kurum taji tana ra ayinsa ranar taci kuka Sam kashe khadija baiyimata ranaba tunda gashi haryanzu Usman baidaina sontaba Kuma baimanta da itah ba dukda abunda boka yace Amman kamardai shidin abun baiyimasa aikiba"" Amman su labila kam aiyayi masu"" Mikewa tayi tahaura sama ranta abace Usman kam baidamuba saima yasake mirginawa yasoma tunanin ruhinsa duk da haryanzu yana tunaninta Amman baisan yazaiyiba Sam yakasa tuhumar kowa yabarwa Allah komai""" Akwana atashi hasarar mai rai cikin khadija yashiga wata Tara komai dakyar takeyiwa kanta"" zaune"" take cikin falo" kamar""daga sama taji muryar Usman yana kwalamata kirah zunbur tamike tasoma waige " jin kiran yayi yawa kawai tafita harabar gidan tunda take bata taba kaiwa harabar gidan ba Hartasa kafa zata fita tatunoda maganar wannan aljanar jiki bakwari tajuya zatakoma taji yasake kwallah mata kirah batareda shawarar komaiba tasakai tafitaa Aisha✍🏼 ☠ *HATSABIBIN BOKA!!!*☠ Chapter 99 By Gentle Lady💃🏽 Tana fitowa sukayi ido hudu da Usman bakinta tadafe tana kuka tana dariya alokaci daya shikuma murmushi yakeyi tace dad Kaine yaushe kazo nan wayafadama ina nan??? Yace haba Deejarh duk inda kike aidole zuciyata tasanardanie Kizo maza mubar dajin nan mugun dajinie"" batareda shakkar komaiba tatunkaroshi gabanta taji yayanke yafadi saikuma tatsaya chak Zuciyarta tanacewa wannan ba Usman bane kaitasoma girgizawa tana jadabaya """ cikin sansanyar murya yace menene kuma khadija kizo gareni mana kinkuwasan halinda nakeciki sanadin kewarki Cikin daga murya tace karyane kaiba dady bane kaiwayee? Meyakawoka wajena "" meyasa kakeson cutardanie"" Jinhakan keda wuya kawai sai aljanie hayyanul zairi yarikida yakoma katon jemage"" mai fika fiki sosai yayi mamakin da khadija ta iyah ganeshi dariya yasoma kyakyatawa wacce tasaka khadija Dade kunnuwanta saboda karar muryarsa dakuma rukukinta yatsaya da dariyarsa yace ke yarinya baki isah kisan koni wayeba abudaya nakeso kisani kafin nashanye maki jini shine nine nan zanzamo ajalinki Yau ina wacce zata taimakeki kikirata kokuma kikirah Wanda zai ceceki daga hannuna yauba makawa zakikwana lahirah Aini taimakoma akamun yauzanyi murna bayan kema Ashe harda kari nasamu yau zanmore dajikinku Khadija tace karyane jinina bazaitaba zama abincinkaba in Allah yayarda yaunice zanga karshenka Allah bazaitaba baka sa a akainaba Tanagama fadin haka tajuya daniyar komawa cikin gidan kamar walkiya yasha gabanta babban kuskurenda yayi kenan shaf yamanta khadija tanayin azkar dasafe babu wani mahalukin aljaninda ya isah yarabi jikinta batareda yakoneba Iska yazama tayanda bakaganin komai face iskan yakai hannunsa yadankota alokacin khadija tasomayin addua dakarfi Hayyanul zairi yarigada yariketa wata wahalalliyar kara yasaki yafada gefe daya hannunsa yasoma dayewa kamar yasaka hannunsa jikin dalma tuni Dan fiffiken dayake gadara dashi yafincike Hakan baisa ya daddaraba kawai yataso gabadaya yayi mata baran makauniya yasake kwamtsa wata uwar kururuwa cen nesa da ita akayi wurgidashi take dukkan ilahirin jikinsa yasoma cidawuta Khadija haryanxu batadaina addua ba cen taji iska yana kadawa maidadi ahankali tabude idonta tayi Arba dashi cen yashe bayako motsi wasu hawaye masu zafii suka saukomata mararta taji tafara ciwo Dakyar ta iyah daga kafa zuwa cikin gidan tanajan kafa tanashiga falo taduke tasoma kuka danciwonda bata tabajin irinshiba""" nantakama murkususu Haryanzu bakinta baidaina ambaton sunan Allah ba""Allah yabata ikon yin numfashi maikarfi saiga kan danda yafito sallama tajiyo cikin gida duk da bushi bushi takeganie Wata dattijuwa ce tashigo dasauri takaraso wajen tataimaka mata tajaye yaron saigakuma wata dabuwar nakuda bajimawa tasake suntulo wani Dan wannan tsohuwar tayanke cibi tawanke yaron tahadamata ruwa tayi wanka Duk wani taimakonda za ayiwa maijego itah tayimata tea tahadamata maikauri tasha takwanta babu jimawa barci yadauketa Saidai tafarka tana tunanin mafarkinda tayi wai wani aljani yaso kasheta Amman sunyi fada baici nasaraba kuma tahaihu harwata mata tataimaka mata tatuno damaganar aljanin dayake cewa yasamu Karin Jinie Hannu tasaka tashafo cikinta kwalelen batagama rufe bakiba taji cikinta wayam dasauri tamike daga kangadon tace innalillahi badai shiru tayi saikuma tasoma dariya ganin jarirai guda biyu cikin shigarsu ta alfarma kowannensu hannunsa yana bakinsa yanata tsotsa Dukawa tayi takuramasu ido kamarsu daya da sahiba kenan Usman sukabiyo murmushi tayi najin dadi kenan ba mafarki tayiba Alhamdulillah Dayan tafara dauka takurama ido tsirarun hawaye suka sauko sai akan kumatunsa saiyabude idonsa yana kallonta yana lumshe ido kamar yasan dalilin kukanta Saman gadon takoma takwanta tarungumesu tafashe dakuka kowanne uba zaiyi gurin a Haifa. Masà yaransa gabansa yakallesu yaga kyautarda Allah yayimasa Tashare hawaye kutaku kaddarar haka tazodashi babanku baisan mada cikin kuba saiyanzu take tuna in tsohuwarda ta tai maketa kowacece Tana kwance harkusan magrib saiga dattijuwar tadawo tasake hadamata ruwa tayiwa yaran wanka tashiryasu takawomata lafiyayyen abinci yaji kayan yajie saida tagama komai tatafi Khadija dakanta tayiwa yaran huduba" takirasu da sunayensu hassan da husainie yaran akwai hakurin yunwa danko alama basuyi kukaba saiwashe gari da tsohuwar tadawo ta umurceta data basu nono Kullum haka takezuwa harsukai sati ranarkuwa tana zaune dasafe tsohuwar tazo bayan tagama shiryasu khadija tace innah matar takalleta da murmushi tace na am"" tace inaso ingodemaki akan taimakonda kikamun Tayi murmushi tace bakomai yata aiyiwa Kaine"" khadija tace innah wanne gida kike?? Tasake murmusawa tace Niger nake kokintaba zuwa cen ne??? Khadija tace ah ah kafin tasake jehomata tambaya hartafita hakadai sukacigàba dazama damatar hartayi arba in Tasoma hadamata maganie akwai nasha nawanka dakuma nahayaki cikin sati biyu khadija tagoge tayi haske fatarta sai sheki takeyi Su hassan sunada wata bakwai sannan dattijuwar nan tayiwa khadija sallama tace itah zatakoma khadija tatambayeta sunanta murmushi tayi tace Hauwa u kafin khadija tayi magana dattijuwar tafita khadija tanata nanata sunanta acikin ranta itakuma wannan aljanace ko mutum??? Amman naga aikinta kamardai irin na mutane sosai khadija tasaba da itah duk da bawai fira takeyi da itah ba Amman tanajin dadin zaman gidan tunda akwai mai tayata zama kuma koda yaran tana rikemata itakuma tayiwa daya wanka sa arta daya basuda kuiya basa kuka yanzun harsun soma tashi tsaye batareda sunrika wani abuba"" khadija idan tana karatun Qur anI saitaji sun natsu kamardai sunsan abunda take karantawa "" bayan watanni biyu datafiyar dattijuwar alokacin su hassan sun iyah tafiya idan kagansu zaka rantse da Allah sun shekara biyu domin jikin girmane dasu gakuma wayo dansun fara magana Khadija Sam tasaba dazaman kadaicin itah Kadai acikin gidan zaune take cikin falon tazaunarda su hassan tanayimasu karatun qur ani Sukaji anyi sallama Kusan tare suka kalli kofar danganin maiyin sallamar wannan aljanarce tashigo cikin murmushi dakuma fara a tanasanye cikin lifaya fara tayafa farar alkibba""" khadija bazata taba mantawa da fuskar taba ta amsa sallamarta tatashi dasauri ta isah inda take tarungumeta saikuma tafashe dakuka Hannu tasaka tana bubbuga bayanta alamar rarrashi cikin kuka tace dan Allah kimiyardani gidan mijina nagaji dazama wajen nan "" tajayeta daga jikinta tariko hannunta suka dawo wajenda su hassan suke tazauna tana kallonsu sannan tayi murmushi tamiyarda kallonta kan khadija tace yagidan ya yaran""" ahanzarce tace qalau muke Dan Allah kifadamun yaushe zaki kaini gida bansan halinda yan uwana sukeba da mijina atakaice inason Yayana suga mahaifinsu Tanisa tace hakane zaki iyah tambayata nikuma ashirye nake inbaki dukkanin amsoshin tambayarki"" Amman kidaure kiyimun tambaya daya daya domin insamu damar baki amsa gamsasshiya"" Khadija tace meyasa aka kawoni nan??? Aljanar tace ai ina tunanin kinsan wannan amsar Amman zansake tunamaki ankawoki nan ne domin akasheki hasalima banan yaso yakashekiba zaikaiki duniyar aljanune datake kasar Iraqi wajenda babu wani mahalukinda zaije cen yadawo daransa saiwanda Allah yanufa kuma yakeda Karin kwana anan gaba Lokacinda yaratso tawannan jejin sakamakon Neman tsarinda kikayi ga Allah lokacinda kika farka shiyasa yafado daga sama kuka fado wannan jejin Khadija tace nandin wacce kasace??? Tace kasar sin"" inajin kintabajin labarinta ko acikin tarihi"" khadija tagyada kai tace tome naimasu sukeson kasheni??? Aljanar tasake gyara zama tace yanadakyau kisan asalin tarihin shugaban wanan aljanin wato *hatsabibin boka* Khadija tace menene alakar tambayata dakuma wannan bokan ina Neman tsarin Allah daga sharrinsa dashi da shaidanun aljanunsa Aljanar tasake murmusawa tace tambayarki tanada alaka da labarinsa zaifi kyau kisaurareni kiji ainahin koshi waye daga cikin labarinsa zakisamu amsar tambayarki shiru khadija tayi batace komaiba Aljanar tasoma kamar haka Tarihin *hatsabibin boka* mukoma bayà wadansu shekaru Dari biyu baya anyi wani kasurgumin matsafi Wanda aduniyar lokacin babu wani boka mai tsananin tsafi dakuma siddabaru kamar shi sunan wanann bokan haiiiiranu wàsu suñamasa lakabida uban shaidanu👹👹👹 Aisha ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠ Chapter 100 By Gentle Lady💃🏽 Bashida imani kokadan sannan kuma yashahara" harwadansu matsafan sukanje wajensa yakowaya masu siddabaru da bokanci azamaninsa babu wani wanda zaijadashi yanada aljanu dayawa wadanda sukaimasa hidima yanada yaro daya sunansa kanzaru"" yanakoya masa yanda akeyin tsafi Lokacinda ciwon ajali Yakamashi"" yatattara dukkanin kayan tsafinsa yabashi amatsayin gado yakara dacemasa karike wannan aikin domin shine kawai abunda zanbarmaka gado Kowanne da yakanyi tutiya dacewa ubansa yamutu yabarmasa gado kudine gidajene filayene dakuma kaddarori tonikuwa wannan din shine abunda nabarmaka kamardai yanda nima nagaji wannan awajen babana shima yagada awajen babansa danhaka karka kuskura kawatsarda wannan Sana a Dan acikinta aka haifeka Lokacinda haiiiiiranu yamutu wadansu bokaye da matsafa sunyita murna saboda Ya addabesu gabadaya aljanunsu suna shakkar sa danhaka ba kasafai suke samun aikiba kowa yafiso yaje wajensa sunyi murna sosai da mutuwarsa aganinsu sunhuta zasu sake suci karensu babu babbaka saigashi kanzaru yazo yakere ubansa da mugunta iyah tsafi siddabaru zalunci harsuke ganin karama ubansa dashi Lokacinda kanzaru yayi nisa yana damawa acikin tsafinsa saiyayi bincike yagano maciji shine zaiyi ajalinsa kuma bazai Dade aduniyaba Yashiga Neman inda zaisamu matarda zatahaifamasa dan da danbayaso yamutu baibar wanda zaiyi gadonsaba"" Acikin bincikensa yagano wata diyar sarkin yan bori akasar Igbo kiristance sosai tayimasa aljannunsa kawai ya umurta suka daukomasa itah yacigaba da amfani da itah batareda andaura masu aureba Saida tashekara biyu sannan tasamu ciki tun cikin yana karami yakeyin tsafi wacikin kuma baiyarda matarsa taci nama dafaffeba saidai danyen nama cikinta yana shiga wata tara"" tasoma nakuda"" yana ganin hakan yatsafeta tasandare dakansa yadayeta yafitarda jinjirin dake cikinta yakwashe jinin jikinta sannan yabawa aljanunsa masu cin nama suka cinye gangar jikin Hikimaryin haka awajensa yanaso Dannasa karyayi tausayi danmuddin yasha nonon uwarsa zaizama maitausayi gawasu Jininta shiyatsafe yadinga baiwa yaron yanasha amatsayin nono lokacinda yaron yasoma girma yalaka masa suna *hatsabibin boka* aikuwa yaci sunansa dankuwa tunyana danshekara biyar yakanyi wani kalar tsafinda ko ubansa bai iyah shiba alokacin yacika damurna danyasan koda yamutu yabar wanda zaicigaba da daukaka gadon gidansu Ko ina na kogonsa akwai hadiman aljanu masu kulamasa dankar maciji yashigo tunda yaga maciji shizaisama ajalinsa yasa akashirya masa wani gado maikyau Kullum zakasameshi akan gadon baya yarda yaje ko ina dangudun haduwa da ajalinsa abunda baisaniba dukkan abunda aka kaddara shine zaiyi ajalinka baka isa ka kaucemasaba Shiwannan boka abincinsa nonon shanu Wanda aka tatsashi yanxu yanzu kuma baya yarda yasha nonon awani guri kohannun wani aljanie sai hayyanul zairi danshi kawai ya amin dashi watarana ya aiki hayyanul zairi diban madara bayan yadibo yanakan hanyar dajin zaikaimasa toshikuma yanajin yunwa saiyayi katari dawadansu fatake sunsamu hatsari akan hanya saiya yanke shawarar zuwa yasamu jininda zaisha Yasamu guri yagirke kwaryar nonon yatafi bayan tafiyarsa da sa o i biyar saiga wani maciji yafito raminsa yanajin kishirwa yanaganin kwaryar nono kawai yakafa bakinsa yasha asheyazuba kuma dafinsa aciki Yayi tafiyarsa hayyanul zairi yana dawowa yadauki nono yakaiwa shugabansa bawani tunani yakafa kai yasha Bayan shudewar rabin awa saidafin maciji yasimayimasa aiki yanajin yanayinsa yasauya kawai yadauko madubin tsafinsa yasoma bincike yagakomai saninkuma ajalinsa Yakama yakirah *hatsabibin boka* yadamkamasa gadon Kujerar mulkin bokanci yasake jaddada masa karyayi wasa dashi danshine zaiyi tinkaho kobayan ransa take yasoma shure shure bakinsa yana fitarda kumfa harrai yayi halinsa Tanisa tana kallon khadija tace daga lokacin *hatsabibin boka* yafara shuka mulkin bokancinsa cikin zalunci dakuma cin amana Bayajin tausayin kowaye akabashi yayiwa aiki saikuma akasamu mutanen yanzu sunada rauni sosai akan addu a karancin ilimi dakuma rashin tarbiya Kezan iyah cemaki babu wani aiki daza abawa *hatsabibin boka* ya gagareshi babu wani aikinda yabashi Matsala samadanaki Tanisa tanamai kallon hassan tace Ku mutane kunada sakaci yawanci sakacinku shine yake jawomaku matsala Ansanardaku tayanda zakunemi kariyar Allah daga dukkan wani abun cutarda hakan yashafi aljanu da mutane irinsu *hatsabibin boka* dankuwa sharrinsa yakere duk wani sharrin aljani Yayi nazari dakuma tunani Dan Adam baida tsawon rai kamarmu aljanu Dan adam duk dadewarda zaiyi yayi tsawon rai bazai haura shekara Dari da ashirin ba Wannan dalilinne yasaka abincikensa yagano wata Yar sarkin aljanu tanahiyar kudancin Nigeria yaturah bakaken aljanunsa suka daukomasa itan Yanaso yayi amfani da itah yahaifi danda zaigajeshi yazamana jinsin aljani yafi yawa atare dashi danhaka zai Dade aduniya yanashuka tsiyarsa Itakuma taki aminta dahakan dankuwa musulmace duk da dagabaya takarbi musulunci tayiriko dashi sosai wannan dalilin yasaka yakaita kurkukunsa dayake karkashin kasa yana ganamata azaba harzuwa yanzu baisamu yardartaba Kuma atsafinsa yagani aladole saida yardarta idanba hakaba bazaisamu danda yakesoba zaisamu yaron jinin bil adama yayi yawa ajikinsa Yanzun haka tana tsare acikin kurkukunsa karkidauka itah kadaice akwai mutane da aljanu dayawa awajen wadanda yakeganawa azaba idan suka bijiremasa acikinsu harda bokaye babu Wanda yasan mabudan kurkukun saifa shi danbaiyarda dakowaba yakance shiko kansa baiyarda dashiba ballantana yayarda dawanie khadija tanisa tace ni wannan gimsasshen labarin ya isheni babu wani abun dadi acikinsa menene ribata tasauraren labarinsa tundashidin ba wani malamibane baikafa tarihin komaiba saina zalunci tanisa haryanzu banji amsar tambayataba saidai kawai cikamun kunne dakikai dawannan tatsuniyar banzar Aljanar ta murmusa tace munkusa ai kisake hakurii Dajinda yake acikin taraba yake Amman yatsafe dajin tayanda kodamutum yatafi bazaiganshiba Saifa idan wajensa kikaje sannan zakisamu damar shiga Shikuma dalilinda yasa yatsafe dajinda yake saboda yagano wadansu yara biyu shune zasu zama ajalinsa Wadan nan yarankuwa sunzo duniya Aisha✍🏼 ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠ Chapter 001 By Gentle Lady💃🏽 Tamurmusa wadan nan yaran bawasu bane face yayanki"" jin hakan yasa khadija tawatsa mata wani mugun kallo tana jansu hassan ajikinta tace wannan aizancen banzane akan wanne dalili zanbar yarana suje wajen wannan azzalumin Wanda bai maida rayuwar mutane abakin komaiba"" Yarana basa bukatar hada idoma dashi Aljanar tace khadija kenan kisani tunkafin kizonan nasanda zuwanki wacce *hatsabibin boka* yadauka kanwatace Khadija tayi saurin Tarar numfashinta tace aiho kicedama dabiyu kika taimakeni ni atunani kinyine saboda Allah Ashe akwai wata mummunar manufa axuciyarki game damu Tace kisaurareni khadija dazan iyah aikin nan wlh datuni nagama da matsalar khadija tasake wurgamata wani kallon tace saikuma akace dole Yayana suzasuyi??? Dayake sune kawai ubansu baisan dasuba??? Toni inason yayana bazantaba turasu wajen wannan mugunba kudakuke aljanu ma yagagareku saiwadan nan yaran dako abinci basu iyah baiwa kansuba Aljanar tace khadija kifuskanci maganata wannan abun banikawai yashafaba hardake Khadija tace nibanda Matsala dashi bansanshiba bansan inda yakeba danhaka kinunamun hanya inkoma gida"" tayi maganar tana mikewa tadauki su hassan Aljanar tace nibazan hanaki tafiyaba Amman kishirya domin yatura bakaken aljanunsa duk inda wadan nan yaran suke adaukomasa su aka she inadai kinason yaranki nandin shine maboyarsu Khadija nasan zakice akan Karen bukatata nataimakeki shinkokinsan wannan bokan shine yayi sanadin mutuwar mahaifiyarki Fateema??? !! Kirjin khadija ne yaharba dasauri tajuyo dahanzari tace waike waye yafadamaki hakan?? inakuma kikasan mahaifiyata??? Tamurmusa gazahiri kuwa dattiijuwar nan wacce takarbar maki haihuwa maisuna Hauwa u to kakarkice"" !!! Dam gaban khadija yasake faduwa haba tadade tana tunanin kamar tasan mai fuskarta ashefa da mamantane suke kama Dasauri takarasa tazauna kusa da itah murya narawa tace toyanxun ina take Dan Allah "" tadafata karkidamu zakije inda take khadija komai dakike gani kaddararrene kakarki tabison zuciyarta Ga abunda iyayenta suka zabamata Amman takafe sai kakanki takeso dasukace tazaba kosu koshi saitace tazabeshi tayi wauta mezaihana talallabasu harsu amince Wannan abun datayi mahaifinta yayita fushi da itah sanadin hakanne kishiyarta taimata magani tabargidan takoma Niger duk da batakoma wajen mahaifintaba saboda furucinda yayimata Akan komai yabiyo baya kartanemeshi gata yargidan sarauta dankoda takoma babantane akan karagar mulki lokacinda tatafi tatafi daciki wata uku haka tayita rainon cikin hartasauka tahaifi yara biyu Mace danamiji Tasake maida sunan mahaifiyarki fateema idan kikaganta bazakice kedin nan bace dankuwa babu abunda yarabaku Namijin kuma Muhammad sunansa duka sunyi aure sun hayyafa Amman basacikin jindadi duk tasanadin abunda mahaiifiyarsu tayi abunkuma saiya shafeki keda kike jikanya"" sumacen din kusan hakane Ranarda nabar nan naturah hadimina yasamoman cikakken tarihinki shine nasamu kakarki nafadamata hadarin rayuwarda kike ciki dukta dalilin kin biyayyarda tayiwa mahaifinta tayita kuka aranar kuma nasanarda itah mutuwar kakanki dakuma kishiyarta Aranar namatsa mata saida takoma gidan mahaifinta tasamu yayanta shine sarki bayan tatafi wajen mahaifiyarta tanemi tayafe mata tasanarda itah duk abunda yasamu yayanta gashi haryanason taba jikarta batajiba bata ganiba mamarta takaita wajen mai martaba bashikoda lafiya Yanaganin Hauwa yasoma hawaye shikanshi yayi wauta baidace danyarsa tayi badaidaiba yayimata wannan horon dama saida yayansa yace baidace aimata hakanba"" yadade abun yana damunsa saidai baisan yazaiyi yanemotaba tunda baisan inda take aureba Dakyar yatashi zaune yayimata alama tazo cikin Dari Dari takara inda yake taduka saikuma tafashe dakuka tana neman yafiyarsa yace shikam aituni yadade dayafemata Yace ina maigidanta?? Anan tadanardashi labarinta tunbayan barinta garin dakuma halinda kike ciki yajinjina Kai lallai wannan abun saiyazama izna ga iyaye dasuke nuna isa akan yayansu yanzu kuduba ba itah datai abunba yashafi yayanta harda jikokinta kuskure gudadaya data aikata Inagamu masuyiwa iyayenmu kallon hadarin kaji kallon gidadawa aimu munwaye"' kallon basu isah ba aini bayaro bane dazasu nunamun Abu maikyau nasan abunda yadace ga rayuwata Waisu dansunyi lokacinsu ana takuramasu muma saisun takuramana subarmu muci zamaninmu mana"" hmmm yammata samari yawancinku duk haka kuke Kusani duk abunda kukaiwa iyayenku lallai kukwana dashirin karbar sakamako kukalli abunda Hauwa tayi kuma da abunda yasameta agurinka zakaga kamar abun bakomai bane nankuwa babban laifune. Tacigaba karkiso kiga yanda ake murna sainunata akeyi gadangi "" satin tadaya agidan mahaifinta yarasu bayan kwana uku mamanta tabi Allah mai iko ashedai darabon zasugana ne khadija tace Allah yajikansu tace Ameen "" khadija tanisa tana kallonta tace haryanzu magana kike akan dangina haryanzu bakibani amsataba menene dalilinda yasaka wannan bokan yakeson kasheni .. Tace bashine yakeson kashekiba shima aikine akabashi tatari nunfashinta tace wayabada aikin akasheni??? Bana fada dakoma bantabacin zalin waniba bantaba hayaniya dawaniba to akan wanne daliline za ace akasheni??? Tayi maganar tana kallon aljanar Murmushi tayi tace bakodaya Amman itah wacce tasadin akasheki tanaganin kintaremata wani jindadin duniya Khadija tatareda dacewa wacece wannan??? Batareda shakkar komaiba tace kishiyarki lubabatu"" Khadija tace ban...ban.banfahinci mekike fadaba"" aljanar tamurmusa tace nace kishiyarki lubabatu khadija tace never wlh nifa kinsani aduhu wacce lubabatun??? Tace ina tunanin bakisan wata lubabatu bayan Itaba kuma Usman bashida wata Mata ayanzu sai itah akan me kike tantamar anya itane kuwa??? Khadija tace saboda itah ce mahaiifiyar labila kinga kuwa nasan bazata cutardaniba"" aljanar tamurmusa tace ke yarinyace khadija ai lubabatu ba itah tai nakudarkiba dahar zataji tsausayinki barimadai infadamaki bayan batanki tasa akaturawa yarta kuma kawarki aljani yahurah mata iskar barci Na sihiri kwananta biyar tana barci yanzun haka bata kasar anturata karatu kuma duk bacikin hayyacintaba Gabadaya yan uwanki sunmanta dake kamardai yanda lubabatu tace bokan yayimasu "" nasan bazaki yardaba saboda kinyarda da itah idan zaki iyah tuna kalaman yarta datake maki zakigane hakan domin itah tasan abunda uwarta take aikatawa Khadija kam bakibude take kallonta"" tace waima kinsan usman yanada da saurayi babba yayan labila ne Amman ba lubabatu tahaifeshiba sunansa kaleed Bayan lubabatu tasa ankashe mamarsa ameenatu tasa kuma boka yakashe kaleed saidaikuma abunda basu saniba acikin aljanunsa akwai wani maisauran imanie saboda lokacinda ana tsoratarda maman kaleed hardaashi cikin masuyimata gizo suna zama kadangaru Aisha✍🏼 ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠ Chapter 002 By Gentle Lady💃🏽 khadija ce tayi saurin Tatar nunfashinta tace waiikina nufin dadyn labila?? Tace sosai kuwa lokacinda lubabatu takeson miji taje wajensa kuma itah tasakashi akashe matar Usman"" shine yatura aljannu sukarika tsoratata karshe aka sakomata ciwon zuciya tarasu bayan nan kuma tasakecewa akashe kaleed saidai aljaninda yaturah yakasheshi kafin yaje wani dagacikin aljanunsa yayi saurin zuwa yadauke kaleed din tareda kayanshi Aka idar *hatsabibin boka* kuma duk yabawa aljaninsa aiki kuskure banaka bane kuma rashin aikata aikin zaijamaka mummunan hukunci Lokacinda yaje gidan baitararda kaleed dinba saikawai yakama bakinshi a zuwan shine yadaukeshi domin bayan yadawo yana taraddadin sanarda *hatsabibin boka* saikawai akabashi kayan aiki saikawai yakarbe kayansa yayi shiru Takai kwarshen maganar tana kallon khadija"" khadija wacce hawaye sukebin fuskarta"tanisa toke taya kikasan dukkan labarinsa??? Aljanar tamurmusa tace kakana shiyayiwa kakan *hatsabibin boka* aiki lokacinda yamutu sai kakana yatuba dalilin wani malami anturashi jikin wata mata domin yahanata zaman aure Awajen rakiyyya da malamin yayimasa wa azi saiya tuba Amman bayada hujjar sanarda kakan *hatsabibin boka* haka"" shine yagudu zuwa makka yayita tura mayakan aljanunsa Amman sunkasa samun nasarar shiga inda yake saboda duk wani mugun aljani bazai iyah shiga wurinba Yanacen har yamutu dansa yasoma mulkin bokanci shima yamutu wannan yazauna lokacinda yadauke Kanwata alokacin labarinsa yadawo farko danmukammu bamusan kakanmu yayizama dashiba kuma akwai wani aljanin abokin kakana dayake wajensa shine yakesanar dashi sirrinsa"" kinji tayanda nasamu labari Saboda yanagudun ranar mutuwarsa yasa matakan tsaro sosai adajin tayanda babuwani mahalukin daya isah yaje dajin inhar bawai dan ayiwa wani maganiba dazaran katunkari dajin komai zaijuye maka zakayita haduwa damiyagun namun jeji karshe sukasheka Khadeeja tace to ahakan taya su hassan zasuje dajin??? Tamurmusa wannan aikinane bukatar bokan banaso tacika khadija kitaimaka kicire sauran mata daga sharrin wannan azzalumin bawan"" khadija tace totaya kenan"" aljanar"" tace bayanxu zasujeba inhar kinyardaa zandaukesu inkaisu wajen kakana har lokacin"" da yakamata suyi gaba dagaba tunda kinason komawa wajen mijinki damadai baisan kinada cikiba saiki koma duk ranarda akagama komai zakiganni gidanki tareda yaranki Tanisa ammanfa zuwanki gida akwai rudani"khadija takwalalo ido tace rudanin menene??? Kardai bazasu ganeniba??? Tace kodaya dazaran sunganki duk Wanda yayi ido hudu dake komai zaidawomasa take asirin zaikarye Saidaikuma abunda sukahada da itah dabokanta sun aje sako azuwan wasune suka saceki kuma sunce kar anemeki"" Dankuwa kasheki zasuyi "" danhaka idan kika koma saikisan yanda zakiyi kisan yanda zaki bullomasu domin kishiyarki *hatsabibiyar matace* tabugawa ajarida tunda nake bantaba ganin bil adama Marar imani kamartaba Sam kamar ba musulmaba"" batada imani kokadan ke intakaice maki labari akan acire sonki acikin zuciyar Usman tabada jinin wadansu jinjirai biyu Khadija tace innalillahi wa inna ilaihirrajiun yanzun mom din tabada jinin jarirai akan wani banzar burinta na duniya??? Tanako tunanin mutuwa??? Aljanar tace bana tunanin haka khadija saboda abunda tayi yawuce saninki ina tunanin bakida labarin aurenda Usman yayi kafin ya aureki?? Khadija tace inazan sani tundashi baisanar daniba aljanar tagyara zama tabata labarin duk matanda tasa aka kashe dakuma wacce takora dakuma wadanda akayita turawa aljanu takareda cewa kece kawai kika Gagari dukkan aljanunsa sunkasa rabarma jikinki Khadija wacce take rusar kuka haikan tace yanzun dady yasan abunda takeyi??? Aljanar tace baisaniba kuma koda fadamasa kikai akwai wahala yayarda domin macijiyace itah maidafi biyu ketafi kunama hadari Duk wanda zakibaiwa wannan labarin azuwan makaryaciya zaidaukeki danbazai yardaba cikikuwa harda iyayen duka kishiyoyinta saboda rabuwar arziki sukai baza ataba zargintaba saboda batabar wata shaidar dayakamata azargeta Takauda hankalin duk wani maitunani mugunyar matace dakike ganinta Nina San koke yanzun kina shakkar labarin nan Khadija tanisa tace haryanzu bangama yarda ba inaganin kamar bazata iya aikata wannan mummunan laifinba Aljanar tace karkidamu bazan tilas taki yarda da abunda nafadaba Amman duk ranarda kika koma zakigane hakan dakanki Dan dazaran taganki zatashiga rudanie kuma tamakara Dan lokacinta yazo da itah dabokanta alkadarinsu zaikarye Khadija tace Toni taya zanfita dajin nan injegida tunda bansan hanyaba kuma wannan mugun aljanin nasan yana nan yanajirana duk sanda nafito Aljanar tayi murmushi tace wanne aljanin?? hayyanul zairi??? Khadija tace nikam inazansan sunansa"" aljanar tace ai khadija kinyimasa illah "" illarda kodama yarayu bazaisake moruwaba inajiwa lubabatu tausayi danhar naga yanda zaidau fansa Khadija Tatari nunfashinta tace mezaimata bakuma kince ita tasaka aturoshiba??? Tace hakane Amman abunda bakisaniba su wadancen aljanun duk akaturasu suyimaki aiki inhar basuci nasaraba akaimasu illah bamakawa jikinka zasudawo saisun fanshe ajikinka Khadija tace yanxun kina nufin zaikoma jikinta??? Tace babu makawa domin gabadaya jikinsa yakone fikafikansa dayake tashi dasu gabaya sun raunata wainikuwa wacce irin addua ce kikai haka??? Khadija tamurmusa tace bankaranta komaiba bayan surori guda uku Na karshen Qur'an masu fara wa da qul Kisani babu wadansu surori acikin qur ani Wanda zakinemi tsarin Allah dasu wadanda sukafi wadan nan surorin aljanar tagyada kai tace kwarai dankuwa sunhada daneman tsari daga sharrin mutum aljan da maihassada khadija tace kinsan wani Abu wlh saiyanzu nake tuna abunda sahiba takemata ina hanata ashedai itah tasan abunda tasani Aljanar tace sosai abunda yasaka takasa sanarmaki anrufemata bakine"" tanisa yanzun kisake zama nan nawadansu watanni kafin su hassan susake kwari tayanda koda kinyayesu baxasu cutuba""khadija tabuga tagumie tace ni wlh kinsa jikina duk yayi sanyi"" anya zansake komawa gidan kuwa??? Aljanar tayi dariya danjin furucin khadija tace kintsoratane??? Khadija taja majina tace bawai naji tsorobane dannasan babu abunda zaisameni face abunda Allah yarigada yatsaramun rayuwata "" kingakuwa ban isah in karkare kaddarata ba Amman gaskiya inajin tsoron wannan matar da sharrinta indai abun nan dakika fada duka ta aikatasu gaskiya tayi nisa saidai inyimata fatan Allah yashiryeta da itah daduk wata maihali irin nata"" Amman gaskiya baxansake komawa gidanba nahakurah dawan nan auren Aljanar tasake darawa khadija takalleta da mamaki tace dariya nabaki??? Tace um um maganarkice tabani dariya shindakike cewa bazaki koma gidan Usman ba yazakiyi da soyayarsa?? Zugum khadija tayi gabanta yafadi tayi shiru" aljanar tacigaba Ninasan kinason Usman sobana wasaba danhaka karkitaba karyarda zuciyarki khadija ninasan wacce zansa tasake maki shiri takuma koyamaki dabarun zaman aure dankedin karamar yarinyace bakisan kirsar mataba"" Zatakoya maki yanda zaki tarairayi mijinki duk da nasan kakarki tagamayi maki komai Amman zansake hadaki dawannan matar dan nayarda da itah sosai zaku zauna da itah nawani lokacin kafin kitafi gida Gaisuwa da fatan alkhairi agareku baki daya banhakuri "" inamai Baku hakuri kunjini sai ahankali kwana biyu biki mukayi shiyasa yanzun dayama kukasamu saikuyi hakuri dashi zuwa gobe nagaida kowa kyauta🙋🏽 Aisha✍🏼 ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠ Chapter 003 By Gentle Lady💃🏽 Khadija tace nifa mamaki nakeji haryanzu jifa yanda take nuna halin ko inkula akan mijinta tamkar batada kishi"" aljanar tace ai mugunyar kenan munafukar boye aikara Wanda zaifito fili yanunamaki Abu dawanda zairika yimaki zagon kasa idan harmutum zainuna maki aike zakisan yanayin takunki dashi Khadija tace hakane kam wlh datacemana tabarmana kwanakinta tausayi tabani nace tanason mijinta sosai harnafara zargin kaina anya banyi shishshigiba nashiga tsakanin masoyan asali Aljanar tace abunda bakisaniba aidabiyu taturaku Dubai saboda *hatsabibin boka* yace muddin kina gidan baza asamu damar yimaki komaiba saboda kullum kinayin azkar Amman idan kikabar gidan kukaje yawon shakatawa hankalinki zaidauku kimanta dayin azkar Tayarda kuje dantasan babu abunda zaishiga tsakaninki da usman kamar yanda akeyiwa sauran matansa """ kuma dazaran kuntafi za aimaku asirinda zaishafeku khadija tayi shiru daga bisani tace wainikuwa bakifadamun sunankiba?? Tayi murmushi tace sunana maimunatu khadija tace masha Allah suna maidadi Tace ko nagode khadija tace mubar maganar "lubabatu "" au momy maimunatu takamayimata dariya tace kibarshidai nafarkon khadija tayi dariya tace ah ah mom din sahibace kinga komai tamun matsayinta yana nan"" Tanisa yanzu maimunatu ya maganar kaleed kuwa??? Inayake ??? Ina zamuganshi tunda kinga shidin baisan danginsaba kuma yazaiyi yasan inda suke"" Maimunatu tace sai angama war ware komai zakidawo dashi gida"" khadija tace toni ina nasan inda yake??? Maimunatu tace yana gidan hassan"" kanin mamanki yanzun haka baya ma kasar yana London wajen karatu Khadija tace ikon Allah shikuma cen aka kaishi?? Maimunatu tace hakane aljanin yakaishi cen"" kuma dakinganshi basaikin tambayaba dankamarsu daya da Usman saidai kawai kice shidin yafishi kuruciya Amman babu abunda yarabasu kamar hassan dahusaini Khadija tace nikam danakoma zanje wajen kakata inason ganin kaleed din nan koba kamai inason yadawo hannun mahaifinsa Maimuna tace akwai sauran lokaci karkiyi saurin sanardashi gaskiyar lamarin kibari saisu Husain sunkara girma kamar nan da shekara hudu saidai zaki iyah zuwa kiganshi koda zakifadamasa gaskiya Amman kifadamasa yasake hakuri kifadamasa shirinmu zai fahimceki yanzun saura shekara daya yagama karatunsa Khadija tace shikenan Allah yakaimu .maimunatu tace Ameen"" duk labarin nan da akeyi su husaini suna zaune bakajin ko motsinsu tamkar sunsan abunda ake fada"" tare sukacigaba dazama gidan yanzun hartakan fita dajin da itah da maimunatu Amman banda su hassan Akwana atashi babu wuya wajen Allah su Husaini sungirma shekararsu daya dawata takwass Amman magana chauchau gasu dajikin girma hargudu sunayi idan kaji yanda suke karatu saika rantse da Allah sunyi shekara biyu aduniya tunsunada shekara dawata biyar suka yaye Kansu danbasa Neman mama saidai abinci hakan yasa maimunatu tace tayayesu Saitakara watanni su Husaini sunada shekara biyu sauran wata daya suyi shekara biyu maimunatu tacewa khadija tashirya zatakaita gun matar Yanxun Sam khadija batayin murna dakomawa gidan Usman dantun ranarda taji komai gameda lubabatu taji gidan yafice aranta tamadaina sakawa ranta tunani Sam batasake nunawa maimunatu tana kewar mijintaba sosaikuma taji dadin zama da itah danzamanda sukai da itah tagano yawan ibadar da takeyi dadere bata barci itama take koyawa su Husaini karatu dan itama tahardace Qur ani Ranardazasu tafi khadija harda kuka tayi narabuwa dasu hassan kunsan tsakanin uwa Dada sai Allah Amman abun mamaki su Husaini basuwani damuba saida tayimasu addua sannan suka fita gidan"" sunafita tacewa Khadija tarufe idonta Batareda musun komaiba tarufe idonta tarike hannunta take suka bace tamkar guguwa tsayin awanni biyar saigasu kofar wani gida Dan madaidaici tsarin gidan yanada kyau batareda bata lokaciba tace munkawo kibude idonki Khadija tabude idonta tasoma kalle kalle tasoma ganin mutane saitayi hamdala dantasan tashigo cikin jinsinta maimunatu wacce haryanzu murmushine kwance akan fuskarta tace Yar uwa nanne gidan matar Kuma nayimata bayaninki duka danhaka komai tace kiyi kiyi karkiyimata musu Khadija tagyada kai"" maimunatu tacigaba yaunakeson mukama hanya dani dasu Husaini saikiyitamana addua Allah yakaimu lafiya dannasan *hatsabibin boka* yana nan yana Neman inda zaigansu danabarki nan zanwuce danhaka karkimanta da abunda nafadamaki karkiyi sanya dazaran kinsauka gidan kisamu kidauko madubin nan kikona aljaninda yake gadin madubin dannasan muddin taganki zata sanardashi daganan zasu sake yimaki wani shirin kamardai yanda suka yaudareki tunfarko khadija tace karkidamu Yar uwa ban manta dakomaiba Tasaki murmushi tace hakan nakeso Yar uwa tomuje taresuka turah kofar gidan tareda sallama"" saida sukai sallama kamar sau uku sannan aka amsa akace kushigo mana Maimunace agaba khadija tana baya aranta tace tofa ashedai harda aljanu sunazama cikin mutane lallai saimuyi taka tsantsan daidai sunshiga falon tana zaune tanacin abinci tanaganin maimunatu tasaki fara a tace kece tafe maraba kushigo mana, suka wuce tanuna masu kujeru tace suzauna taresuka zauna sannan sukasoma gaisawa Tace yahanya Yar uwa maimunatu tace alhamdulillah tace hajiya gatafa nakawo tayi maganar tana kallon khadija matar tayi murmushi tace ainagane Amman maimunatu ai Yar uwartaki ma da damarta baza asha wata wahala akantaba"" tace hakane gatanan dai nakawo maki kiyimata gyara na musamnan sannan kikoyamata yanda ake tarairayar Miji inason idan takoma yadauka wata sabuwar khadija ce aka kawomasa Kusan Tare suka sa dariya tace karkidamu kinyi dashe gida mai albarka inamai tabbatar maki dasaitafima yanda kikeso"" kedai kawai kibar komai ahannuna"" maimunatu taciro jakarta tadauko kudi tace gacikon kudinki"" nizantafi tace to maimunatu Allah ya kiyaye hanya khadija tataso sukafito Bakin kofa suka tsaya suna fuskantar juna maimunatu tace to khadija nizan tafi "saina dawo maki dayaranki insha Allah zancika alkawari zanyi iyakar kokarina inkaremaki yayanki saiki tayamu da addua Allah yakaremu"" khadija tace Ameen nagode sirarun hawayenda suke cikin gurbin idonta suka karasa gangarowa tace zanyi kewarki sosai ashedama anasamun aljanu masu son mutane nibanyarda dahakanba saiyanzu Maimunatu tayi dariya har hakoranta suka bayyana tace ai khadija kamar yanda kikasan acikin mutane akwai mugaye salihai nakwarai yan iska dasauransu komai kikasan za asamu acikin jinsinku muma akwaisu anamu Khadija tace Yar uwa yanzun wannan ma aljanace??? Amman naga tanacin abinci irin namu Amman kenaga bakyaci Maimunatu tasake darawa tace mutumce kamarki bakiga tayi kama da jinsinkuba"" khadija tace aibanganewa aikema babuwanda zaice kedin ba bil Adama bace Amman Ina mamakin ya akaitasanki Tace nima nasantane wajen wata Yar uwata takebamu labarinta duk sanda zanzo wajenta nakanyi shigar bil Adama kamardai yanda kikeganina itama haka danba ainahin siffata kenanba khadija tajinjina kai tace tonikam nandin wanne garine??? Maimunatu tace Maiduguri ainasan dai kinsan garin kobaki taba zuwaba kinada labarin garin yanzun gakudi tayi maganar tanazuge jaka tabata kiyi amfanie dasu kikoma gida idan hajiya tarana tagama sallamarki Dan Allah kuma idan kinkoma kiyi amfani daduk abunda tasanar dake karyazama anfadamaki Abu kirikajin kunya danbabu kunya kikyautatawa mijinki inhar karace kikewa labila yanzun kinsan matsayin lubabatu danhaka bata chanchanci kara awajenkiba Khadija tayi murmushi tace bakida matsala dawan nan zanyikomai kodan natusa mata takaici nimadinfa bata wasabace wlh irin rayuwarda nashiryawa kaina bagaskiya bane Amman danatuno mahaifin kawatane sainaji kunya banaso yadauka nidin banda kunyane Maimunatu tace babu wannan khadija kinga barinayi sauri yana jirana" khadija taleka waje tace wayene yakejiranki?? Ina mukawaine mukazo nan?? Maimunatu tace ah ah aini banda isasshen karfinda zandaukeki inyi tafiya dake saboda karancin karfina danice zankawoki nan saimunyi kwana uku ahanya Saurayin Kanwata wacce take hannun *hatsabibin boka* shine yakawomu yanada masifar sauri yanzunma. Abunda yasaka mukadan jima ahanya nace yayi ahankali sabodake khadija kam tasake tsurewa da al amarin aljanu Aisha✍🏼 ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠ Chapter 004 By Gentle Lady💃🏽 Khadija tace shikenan Allah yakaiku lafiya yatsareku" maimunatu tace Ameen Sannan tasakai tafita khadija tana tsaye saida taga tabace sannan tajuya cikin gidan jikinta sanyaye"" Tashiga da sallama hajiya tarana ta amsa mata sallamar tashiga tazauna hajiyar tace yata bari nazubomaki abinci kici saikije kiwatsa ruwa kisamu kihuta gobe saimu fara dankar akure lokaci Khadija tace inaso nayi sallah ne tace badamuwa muje innunamaki dakinda zaki zauna bamusu tamike tanagaba khadija nabinta wasu dakunane kusan guda biyar Jere dajuna tabude mata daya tashiga tana biyeda itah dakine maikyau kayan dakin madaidaita naxaman Mace daya tace gabandaki cen gakuma abar sallah nanne gabas saikiyi hanzari gashi ankusa magrib Khadija tace to tacire mayafinta tashiga toilet din sannan hajiyar tafita bayan tafito tashinfida abar sallah tarama sallarda akebinta tatsaya lazumi tanamai rokon Allah yakaremata yayanta kuma yabasu sa ar abunda zasuyi Tana zaune saman abar sallar har akayi magrib hajiyar tanakan lekowa saitasamu tana laxumi saita koma bayan tayi magrib bata bargurinba saida tayi isha i sannan tawatsa ruwa koda hajiyar tashigo tasamu khadija tana miyarda kayanta tace tafito taci abinci tace to bayan tashirya tafita tasameta falon zaune tagaida itah ta amsa cikin sakin fuska tanuna mata abincin tadauka tasomaci tuwon shinkafane damiyar kubewa tasha kayan yajie saikuma maganie da akasaka aciki da bisimillah tasomacin abincinta hartakoshi tabata ruwa tasha ruwankam badadi ace war Khadija dafarkoma tadauka lemune saida takai bakinta kamshin kayan yaji yadaki hancinta aranta tace kilanta wani hadin lemune maidadi saida harshenta yadandana tagane komeye tasha iyakar shanta Hajiyar takarba tamiyar a fridge tace kingansu nan koda zakiji kishi dagayau sune ruwanki batareda musum komaiba tace to fruit tadaukomata anyankasu kana na kana na sunsha madara gashi dasanyi daidai gwargwado Tabata tace tasha shima duka tashanye sundan taba fira yawancin maganar duk hajiya keyi khadija iyakarta eh ko ah ah saikusan goma tayimata sallama tace taje takwanta tayimata saida safe tashiga dakinta alwala tadauro tasomayin sallah Al amarin *hatsabibin boka*kuwa tunranarda aka haifi su hassan dajinda yake ciki yasoma girgiza al amarinda yatashi hankalinsa sosai dasauri yajawo madubin tsafinsa yasoma bincike aikuwa dama yasan alamun dayaganie na haihuwarsu shine yabayyana kenan sunshigo duniya Lallai dolene yagansu tunkafin sugirma yakashesu yadukufa nemansu acikin madubin tsafinsa Amman abun mamaki andai nunamasa dajinda suke Amman bayaganin komai yayita turah aljanunsa dajin Amman basaganin yaran hakan yasaka ya ce tokodai sudin ba mutane bane kokuwa dabbobine Madubin tsafinsa yatabbatar masa mutanene kuma suna nan cikin koshin lafiya hankalin boka inyayi dubu yabachi yayimatukar tsorata da al amarin wadan nan yaran tundaga lokacin yasoma bincike hanyarda zaibi danyagansu Yagano dajinda suke tsafaffen dajine babu Wanda zai iyah ganin abunda yakecikin yayi bakinciki matuka yasoma kururuwa wacce taisanadin firgitar duk namun jejinda suke zaune dajin sukasoma yankan nakare Saigashi yaukuma dajin yasoma girgiza tamkar ana girgizar kasa "" *hatsabibin boka* tuni yatsure yasake shafo madubin tsafinsa yanawadansu surutai saiga wani wargajin aljanie asararin samaniya yanagudu tareda wata aljana Amman Sam baiga wasu yara ataredasuba"" Amman nadubin tsafinsa yatabbatar masa lallai sunatare dasu kuma sunkusa shiga saudiya muddin yabari sukashiga tosuntsira Lokacinda zasufito kuma shine zaizama ranar ajalinsa yayiwani gunji yace karyane saidai ninaga karshensu Take ya umurci wani aljani kankabusa yayi sauri irin Wanda baitaba yin irinshiba yacinmasu yanzun yadawomashi dasu bayanshi Kuma yaturah tawagar aljanu Batareda bata lokaciba suka zama iska sukatashi sama sukabaza hanyarda *hatsabibin boka* yanuna masu aljaninda yake dauke da aljana muimunatu yakalleta yace rankiyadade inajifa aljanun *hatsabibin boka* sunabiye damu dannasoma jin kamshin iskarsu kinkuwasan wannan aljanin yafini gudu sosai niko rabin rabin saurinsa banyiba inajin tsoro karya kamamu nibakaina nakejiba yaran nan damuke dauke dasu Maimunatu tace kacigaba da tafiyarka ninasan Allah yana taredamu domin yanxun haka nasan mahaifiyar yaran nan batayi barciba tanakan rokon Allah yakaremu daga sharrin wannan azzalumin Dayardar Allah lafiya qalau zamu isah aiyanzu baiwuce tafiyar yini daya mukaiba yace hakane rankiyadade saiyasake dage fukafukansa ya auna cikin gajimare saigashi yanagudu tamkar jirgi yamaso yafi jirgin gudu shikanshi yayi mamakin saurin nashi Al amarin *hatsabibin boka* kuwa sanda yaturah aljanie kankabusa yabi bayansu aljana maimunatu yanazaune gaban madubinsa yana kallonsu"" duk abunda suke fadakuwa yanajinsu kamar walkiya yaga sunkara gudu dasauri ya umurci aljani kankabusa yasake karfin gudunsa iyakar gudunsa yacinmasu dankar suwuceshi Aikuwa shima yakara gudu tareda tawagar dasuke bayansa kafin sushafe sa aguda harsun cinmasu koda aljana maimunatu tawaiga tayi arba dasu tacemasa yakara sauri gasu abayansu Yace iyakar karfina kenan rankiyadade saidai suzubawa sarautar Allah ido" Khadija tana gama sallah tadaga hannunwanta sama tasoma jero addua tanakiran sunayen Allah taname kaskantarda kanta tanamai yakinin cewa Allah zaikarbi adduar ta take hawaye sukasomaa zuba akan fuskarta Allahu Akbar Allah majirokon bawansa saura kiris tawagar aljanun *hatsabibin boka* sutari gabansu saigawani iska maikarfi yataso Wanda sukansu basusan daga inda iskan yatasoba gashi balokacin damuna bane take iskan yasoma jansu baya baya fukafukansu sukakasa yimasu rana tunisu aljana maimunatu sukabace cikin iskan kafin sa o i ashirin suka kai sunashiga garin makka sukayi hamdala Al amarin *hatsabibin boka* kuwa lokacinda abun yafaru madubin tsafinsa duhu yayi Na wadansu sa o"I sannan yadawo daidai saidai baiga aljana maimunatuba saitawagar aljanunsa Tashin hankali kam Wanda yashiga basai anfadaba lallai dolene yasake wata hanyar danganin yakashe wadan nan yaran saikuma yashiga binciken hanyarda xaibi Hanya dayace akanuna masa itace kawai xaibi danyatsira hanyar itace yasamu yakusanci wannan aljanar datake boye akarkashin kasa wato kanwar maimunatu Dazaran tasamu ciki danda zatahaifa zaikasance musulmi shine xaishiga har kasa maitsarki yakashe yaran komai kankantàrsa Al amarinda yatsoratarda *hatsabibin boka* danyasan dakyarne aljana murjanatu tayarda da bukatarsa kuma gashi ance karyayimatà dakarfi saidason rantaa Yanzukuma saiyasamu hanyarda zaibi danyashawo kanta cikin saukiii Washe gari bayan khadija takarya hajiyar takiratà sukazauña cikin falon tasoma magana kamar haka khadija nàsandai kinsan dalilin kawokinan dayar uwarki tayi Kafin mujekan gyara yanadakyau kisan wani Abu "" duk abunda zanfadamaki karkibar kodaya nafarko kikasance mace maiyawàñ ibada yinhakan Allah zaisake cusa soyayyarki axuciyar m[truncated by WhatsApp] ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠ Chapter 005 By Gentle Lady Abu na biyu kuma tsafta ki kisance maiyawan tsafta kekanki zakifijin dadin jikinki idan kikajiki kina zuba kamshi dakinki yana kamshi Turakar mijinki yakasance duk ranar girkinki kigyarashi kigoge abunda yakamata agoge kiwanke nawankewa kishare kisauya abunda kikasan yadace asauyashi Kigyara ko ina kikunna turaren wuta toilet dinsama haka kiwanke kigyarashi"" sai Abu na uku kwalliya"" kikasance kinamai yin kwalliya dakuma kyalkyali duk abunda kikasan mijinki yanaso idan harkinyi abun zaiyi farinciki tokinuna kinfishi son abun duk shigarda kikasan mijinki yanaso tanadaukar hankalinsa tokirika yinta karkice waike kinajin kunya garin jin kunyarki zaki cutarda kanki Kodakuwa kinaganin yagirme maki sosai aidakunya kiyi Abu gabansa inaso akoda yaushe kirika sakawa aranki da mijinki kike kuma tamkar danshekara ashirin kamar yadda budurwa zatayi da saurayinta kema kidauka kamar hakanne Kar kunya tasaka ki cuci kanki kicuci mijinki" "" Abu na hudu girki karki kuskurah kibari wata katuwar mata tadafawa mijinki abinci inharma baki iyaba nizan koyamaki yata Amman karkibari mai aiki tadafa abincinda kikasan mijinki zaici Koda kunada yawane mai aikin tadafa nagida namaigida kuma kitashi dakanki kidafa masa hakan zaikaramaki kima a idonsa Menene amfanin mujinki yaji dandanon girkin wata banakiba bakida kishi kenan harmayarika santi idan mai aikinku ta iyah girki sosai"" nasandai bazaki rasa iyawaba Amman daya yau zamufara shiga kitchen dake in soma koyamaki Abu nahudu iyah magana kikasance maitaushin lafazi idan kinatare damijinki yazamana yawan shurutuma baidamekiba duk maganarda zatafito bakinki yazama mai amfanice agunki dakuma shi" Maganar kishiyarki kuwa babu ruwanki ke bawai dadyn kawarki bane koda ace matar tatabayin kishi da mamarki karkiji kunyarta kizage damtse kirungumi mijinki kinunamasa soyayya wacce baibata shan irintaba ki aje kunya agefe bayan yafita kidauko aburki dankunya adon yamace ne inafatar kingane bayanina Khadija tagyada kai alamar tagane"" hajiya tarana tace yanzun bari mubarshi haka tashi muje daki zan nunamaki yanda akeyin kwalliya Bamusu tamike suka shiga wani dakin kayane gasunan nakwalliya kamar hauka dakuma kayan sakawa tayi zaune tayimata kwalliya Yar ubansu sannan tawanke mata tace tasakeyi taganie Dayake khadija tanada kai sosai saigashi tasake maimaita kwalliyar harma tafi wacce hajiya tarana tayimata Aka koma bangaren dressing kuma kananun kaya suna karbar jikin khadija duk kalarda tasaka saikaga tasake kyau kamar daman dansaboda itah akayosu talkama masu tsinie damadai khadija bata iya sakasuba Dan takalmanta duka yan kasane flat"" ansha wuya kafin tama iya tsayuwa akansu Kwana uku tanakoyon tafiya dasu saigashi ta iyah harma tanayin gudu "" dasu aka koma bangaren girki Kullum sunacikin kitchen anakoyamata kalolin abinci saida suka kwashe sati biyu suna wannan aikin karkuso kuga khadija tayi jawur kamar kakwanta jini yafito saisheki take gabadaya gidan kamshintane dazaran tawurga zatabar tsarabar kamshi" cikin yan sati uku khadija tadawo ainahin khadija itakanta tasan yanzu tasauya ana saura kwana biyu takoma kaduna hajiya tarana tadauko maiyin Zanen lalli tayimata Zane Dan ubansu"" yayimata daskuwa ajikinta gashi janda akazana shima yafito das Masu gyaran kaikuma suma sukayi nasu saikuma hajiya tarana tacigaba danata nagyaran jiki habawa khadija tasha dilka tasakeyin kyau ranarda zata tafi hajiya tarana tasa akayimata biza taxuwa kaduna dankarta shigo motar haya .tasake jaddada mata komai tahadamata turaren wuta dakuma najiki dakayan mata data hadamata masu inganci tacekuma kartayi wasa dashan fruit ranarda zata tafi har airport hajiya tarana tarakata tareda kayanta duka dama acikin kudin aikintane akasiyo kayan da takalma Khadija tarungumeta tanakukan rabuwa hajiya tarana tace haba yata yaufa ranar murnace kidaina kuka aibamu rabuba ga katina duk sanda kikaso ganina saikizo koki kiranie tawaya mugaisa"" Khadija takarba tana godiya sukarabu suna dagawa juna hannu hajiya tarana batabar wajenbà saida taga tashin jirginsu Khadija kam tuni jikinta yayi sanyi tundasuka shiga jirgin tamakure waje daya harjirginsu yasauka Kaduna tashar adaidaita tadauka zuwa unguwarsu Tundasuka shiga unguwar tasoma kalle kalle damadai bawani dadewa tayi cikintaba tunda bata taba fitaba tunda aka kawota saifa ranarda sukaje Dubai kuma amota suke Amman duk dahakan taga unguwar tayimata haske takara kyau kamarba unguwarba Kofar gidan tacemasa yatsaya tasomabin gidan dakallo yana nan tamkar sabo daganie sabon fenti aka sake yimasa Tadauko kudinsà tabashi tadauki kayanta ta tunkari kofar gidan taturah maigadine yayo zumut yatare kofa yace yammata lafiya ??? Kewaceçe kuma da izinin waye kikazonan Khadija tayi murmushi tace baba wajen mom nazo yargidan nan labila Usman itace tabani sakodaga makaranta inkawowa mom Yayi shiru sannan yace kintabbatar??? tasakeyin murmushi tace inhar bakayardaba zaka iyah sanarda mom din Yace ah ah tundadai kince yarlele ta aikoki ainabari ki shiga inbasonake akoreniba yayi maganar yana budemata kofa yace afito lafiya tace tagode tasakai tabi hañyarda zata sadata da falon shiga gidan Yan aikin gidan saibintà sukeyi dakallo sunga bakuwar fuska Kaitsaye takutsa kanta cikin gidan tareda sallama lubabatu tana zaune cikin falon tahakimce tana kallo sallamarda akayine yasaka tadago fuskarta takalli maisallamar tareda amsa mata bawai dantagane wacce tayi sallamarba Khadija tabita da murmushi tace mom sannu dahutawa"" bakisake luababatu tace yauwa Amman yata banganekiba"" khadija datake tsaye rike da akwatin kayanta takaraso gaban lubabatu tace mom nicefa khadija bakigane niba ina sahibata Kafin khadija tarufe baki lubabatu tazama tatsaye taja baya dasauri tace karyane wakika taba ganin yamutu yadawo "" kinzama fatalwane Khadija ta aje jakar hannunta tace kitabani kitabbatar nidin ba fatalwa bace tayi maganar tana tunkararta aikuwa lubabatu takwamtsa ihu saigashi tasulale kasa asume Dasauri khadija takarasa wajenta tana jijjigata saikuma tatuna damagar maimunatu lallai wannan itace kawai damarda zatasamu tashiga dakin lubabatu kafin ta farfado Dasauri tajuya zuwa kitchen tadauro alwala tasamu wani cup tadibo ruwa tazauna tasoma yin addua acikin ruwan tsayin mintuna goma sannan tafito tasake kallon lubabatu tana nan yanda take batako motsi dasauri khadija tahau na urarda Zata sadata dakin lubcy tanazuwa taturah kofar tareda bisimillah tana .mai sallama kuryan dakin tawuce kaitsaye tana dube dube Inama zataga madubin abunda Baka ajeba aibazaka daukaba Amman hakan tayita nema budacen leka cen hartakai kan drawer din karshe taturah hannu tabude kawai taga wani bakin hayaki yanafitowa tajikin kusuwar drawer din tuni khadija tamatsa baya gabanta yana faduwa duk da taji tsoro kawai dakewa tayi hayakin yatattara waje daya kafin yarikida zuwa siffarsa khadija tayi bisimillah tareda kabbara tawatsa masa ruwan adduar aikuwa watsawarta keda wuya take aljanin yakwallà ihu Wanda yayi sanadin saka khadija toshe kunnuwanta take hayakin yasoma kamawa dawuta haryanzu baidaina kururuwaba zuwa cen hayakin yabace bat Cikin tsoro tsoro khadija tabude drawer din saitayi Arba dakaramin akwati tadauko akwatin tayi bisimillah tana murda kwadon yabude Saiga madubin cikin akwatin yana kyalli tamkar zinari hannu tasaka da addua tadaukoshi kasa ta ajeshi ragowar ruwan adduar tazuba masa Saigawani bakin hayaki yana fita tajikinsa take dakin yasoma girgiza yana juyawa ""Khadija tacigaba da addua saida hayakin yabace komai yakoma daidai sannan khadija tamiyardashi inda yake tamaida kwadon tarufe tasaka a drawer din tarufe sannan tafito dakin.. Hartayi gumie saboda tsoro haryanzu kirjinta baidaina dukan uku ukuba" tasauko kasan tasake shiga kitchen din tawanke fuskarta tadibo ruwa tadawo falon sannan tawatsa mata ruwan Saiga lubabatu tatashi firgigit"" ganin khadija kusa da itah yasa tadaddage zatasake kwamtsa ihu khadija tarufemata baki tace haba mom menene na ihu nafadamaki Ban mutuba daraina mutanenda suka saceni sundauka namutu dasuka ganamun azaba saisuka yardani cikin wani dajie Wadansu fulanine suke tsinceni sukakaini gidansu acen sukaimun maganie harnawarke kiyarda Dani danidin fatalwace aibazaki iyah tabaniba Lubabatu dai saibin khadija taceyi dakallo kamar zararra khadija tasakarmata murmushi tace bari nadangyara bangarena nasan yayi kurah tayi maganar tanajan Jakarta tahau na urarda zatasadata bangarenta hawana hudu lubabatu tabita dakallo tahadiye wadansu miyagun yawu masu dacin gaske.. Batasan sanda tabarke d[truncated by WhatsApp] ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠ Chapter 006 By Gentle Lady💃🏽 Takunda khadija takeyi da takalmanta masu tsini suna amsa kuuwa kwas kwas kwas harcikin zuciyar lubabatu takejin takun Zaune take dirshan tana darzar kuka hardasu majina wannan wacce irin hatsabibiyar yarinyace Usman yahadu da itah???ayimutum magani baikamashi tsafinta yazarta nata duk hanyarda akabi danganin bayan khadijar ace kuma tana raye ?? Indai hakane lallai *hatsabibin boka* yayimata karya dayace ankasheta dankuwa ta tabbata Wanda yamutu baya dawowa tomeyasa kuma khadija tadawo Tadafe kanta lallai dolene tasan abunyi gashi yanxun rana tayi tsaka *hatsabibin boka* yahanata ziyararshi irin wannan lokacin dole tayi hakuri zuwa dare tacigaba da kukanta Bangaren khadija kuwa tanahawa saman tasoma dariya dansosai lubabatu tabata dariya yanda tatsure kamarma harda fitsari tayi awando yanda khadija tayi Tsammani zatasamu dakin tada kurah saitaganshi fes alamu sun nuna akwaimaiyin rayuwa acikin dakin Aranta tace Kodai Usman aure yayi???🤔 Tayi saurin girgiza kai baxaizama hakanba danaji azuciyata tasoma bin dakunan dakallo kayanta suna nan saikuma kayan Usman hakan yanunamata kenan dakinta yadawo tausayinshi yakamata Afili tace Allah sarki hubbyna gani nadawo gareka kayanta tayimasu mazauni tahau gyaran dakin batawani jimaba tagama tunda bashida wani datti tafesa wanka riga da siket tasaka nakanti sun kama mata jikinta hula maitaushi da adon gashi kamar jikin mage tadorah akanta tayi mata kyau sosai tagabatarda sallar azahar bayan tagama. Laximie taninke abar sallar tasako takalmanta tasauko kasa Falon tasamu lubabatu zaune amman yanzun tadaina kuka batadamu dakallon inda takeba tayi hanyar kitchen din tadauki duk abunda take bukata takunna gas tadorah dahuwar indomie cikin mintuna ashirin takammala tadawo falon tazauna tace mom bisimillah Lubabatu wacce takebinta dakallo tace ah ah nagode kici abunki khadija batasake cewa komaiba tacigaba dacin abarta hartakoshi tamiyarda kayan kitchen jin ansoma kiran la asar tahaura sama Bayan tayi sallah tazauna falonta batasake saukowaba hardaare bayan tayi isha"I tashiga toilet tasake Daukar wanka tadade tana tsara kwalliya sannan tajawo akwatin kayan lefenta kananun kayanda usman yasiyamata acikinsu tadauko tayita dubasu daibayan daya Kowacce tadauko saitaga kamar batayiba saitadauko wata karshe wasu yan kantin tadauko Riga dawando wandon baikai kasaba dakadan yawuce guiwarta gefensa yanada wata yarsarka maikyau tana kyalli kamar zinari rigar farace mai Karamin hannu kamarna bes '' gashin kanta tataje dama yasha gyara bakin ribbon tadaureshi dashi saitakawo hula baka tadorah saman kanta daga sama tadan karkace hular gefedaya Takalma farare tadauko masu matsakaicin tsinie tadauko turarukka tasoma feshewa ajikinta daidai lokacinda taji dirar motar Usman takalli agogo taga karfe Tara daidai sweet dinda hajiya tarana tabata tabude jaka tadauko daya taballe tasaka bakinta sannan tasauko tahau na urarda zata sadata kasan ****************** Tana saukowa Usman yana bude kofa lubabatu wacce takezaune tamike tana kallon khadijar cikin mamaki sam khadija batama lura da itaba . Ido hudu sukai da Usman yakuramata ido tundaga sama harkasa yake kallonta kirjinsa ya tsananta bugawa jakar hannunsa ta subuce tafadi hannunsa yana rawa yanunata dadan yatsa yace de de Deejarh na kece?? Kodai gizonda kikasaba yimunne. Hawaye takeyi tanakuma murmushi tace hubbyna Deejarh nkace inanan daraina banmutuba nadawo gareka "" Usman yace dagaske ba mafarki nakeyiba farincikina ne yadawo tashare hawaye tanamai gyadamasa kai Hannuwansa yabude yace taho gareni inji dimin jikinki deejah na danna tabbatarda hakan"" khadija taruga tafada jikinsa yagame hannuwansa yakankameta ajikinsa.. Saikuma tafashe dakuka maitsuma zuciyar mai saurare "dasauri Usman yadagota daga jikinsa yana tambayar lafiya kumatunta sunarike cikin tafukan hannunsa idanuwansa shima sunyi jawur yace me.. Me...akaimaki Deejarh na Dan Allah kidaina kukan nan"" tadago idanuwanta masu zubarda kwalla tace hubbyna dole nayi kuka nayi kewarka sosai tasake rungumeshi tanacigaba da kukanta Yasake kankameta kamar Wanda zaimiyarda itah ciki yace nima haka Deejarh na wlh nayi kewarki fiyeda tunaninki banada wani tunani bayannaki narigada nayi bankwana da farinciki ashedai zakidawo gareni nagodewa Allah yadago fuskarta dasauri yace inafatar basu cutarmun dakeba Hawayen fuskarta sunazuba tace ai Allah baxaibariba soyayyarka itace tasaka haryanzu nakasance ina raye Allah bazaibari ba bazaitaba basu damar cutardaniba Inasonka sosai mijina"" I love u so much hubbyna you are my persistence u are my life "" i really miss u dear tasake shigewa jikinsa murya narawa yace nima inasonki sosai Deejarh na please stop cry"" Shafar kanta yakeyi tamkar yar bebe Amman kukan khadija kamar cewa yakeyi takara"" dago fuskarta yayi dasauri kafin tayi aune tuni yahade bakinsu waje daya yasoma tsotsa kamar yasamu sweet """ idanuwansu arufe suke kowanne kirjinsa harbawa yake tuni khadija tadaina kuka sai ajiyar xuciya datakeyi tama manta wacce duniyar take Hajiya lubabatu maikan doya 🙈tsaye take kamar mutum mutumie tuni tasandare jinin jikinta yadaina gudana kwakwalwarta tadaina aiki nawucin gadi gabadaya masarrafan jikinta suka tsaya chak Usman da khadija tuni tsayuwa ta gagaresu Usman jikinsa saibari yakeyi kawai yasunkuce khadija yadorata akan kafadarsa yawuce sama"" itakuma tayi lamo akafadarsa baisauketa ko inaba sai akan gado yarufamata baya sukadorah daga inda sukatsaya to masu karatu aganinku *nizan iyah fassara adadin zumudin wadan nan ma auratan??? Musamman usman nasankoda nafada tokuwa zanfadi badaidaiba dankuwa zumudinda yake kodarenda yasoma sanin khadijar baiyi hakanba nikam hardariya yabani Baiwani tsaya tambayarta ina suka kaitaba kawaishidai ayiharka Kodayake yabanie tausayi tunda nasan halin lubabatu maikan doya""tunkafin aje ko ina Usman yasoma surutai da alamu bayama cikin hayyacinsa dasauri nafito najamasu kofa Hajiya lubabatu kuwa tana nan kamar andasata saicen tazaburah kamar wacce tasuma tadawo taduba batagansuba aranta tasoma tunanin to yaushema sukabar wajen?? Take tasoma tariyo abunda yafaru akanta dalla dallah tagama tariyar har lokacinda Usman yahade bakinsa Dana khadija lokacinne wutar jikinta tadauke komai najikinta yadaina aiki"" sharaf tazube akan kujera kamar kayan wankiiii *Gaisuwa dafatan al khairi agareku yan group din 🅿harty novels (SUZ) sakonku ya iso gareni nakuma gode da soyayyarku nima inasonku sosai " soyayya marar adadi Allah yabar kauna* *Sauran masoyan wannan littafin inagaidaku musamman rabie da bilkisu " fateema "miss zuhura"Aisha shafa atu zurmie" maryam" yar lele dakuma anty ameena soyayyarda kukeyiwa wannan novel din bazai faduba damadai sauranku fatana daya Allah yasadai basaboda nishadi kukesonsaba Allah yasahaka[truncated by WhatsApp] [3/26, 8:34 PM] Nabila Elharun Q: ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠ Chapter 007 By Gentle Lady💃🏽 *sakon gaisuwa zuwaga friends an novels group (S U Z) ina gaidaku baki daya nagode da soyayyarku* Hannu tadora aka kamar wacce takeshirin kwallah ihu kilantama shidin taso kwallawa saikuma tafasa dankar tatonawa kanta asiri da alamu khadija batasan komaiba tunda bataga wani alamun dasuka nuna khadijar tagane itah ce tasaka akashetaba"" Yanzun kenan yazama dole tazuba masu ido ?? Ina bama zaitaba yiyuwaba babu wata yamace dazanbari tarabi mijina tayi maganar tanamikewa dasauri tahau na urarda zatakaita bangarenta hartanacin tuntube garin sauri Tanashiga tanufachi inda madubin tsafinta yake tabude tadaukoshi tanamaiyin murmushin mugunta dantasan *hatsabibin boka* bazairasa mafitaba"" Shafashi tayi tare dakiran sunan hatsabibin boka "" tayi shiru tanajiran yabayyana har akashude awanni biyu babu alamar sa tace yahaka kodai wani abun yadaukemasa hankali barinabari sai anjima tasake miyarda madubin takoma gefe tabuga uban tagumie Kamar wacce akece babanta da mamarta ne suka mutu"" hawayen bakincikene suka soma zarya akan kuncinta zuciyarta tanamai kuna da tususi kamar zatakama dawuta musamman idan tatuno yanzun Usman yanatare da khadija komesukeyima oho indai cin amanata yake wlh banyafeba😩 Al amarin usman kuwa yau harda kuka yayiwa khadija domin abunda baitaba jiba shiya tsinci kansa acikin yanayin sambatu kuwa saida khadija tarufemasa baki"" yaukam yadarji deejarn sa sonransa abunda lubabatu take hanamasa kamar wacce zatayi kwalliya dashi gashi yasamu saida yagaji dankansa yasaurara mata sannan yajata ajikinsa yana shafar sumar kanta saiga hawaye suna zuba sharr akan kumatunsa Saida sukazubo ajikin khadija tadago dasauri takuramasa ido shima itah yake kallo yatsanta tasaka tana gogemasa hawayen tace . My hubby wannan kukan dakakeyi wlh sainaji kamar bakayi murna daganinaba" "" takai karshen maganar tana sanne kanta kasa Hannunsa yasaka yadago habarta yace kokadan bahaka bane karkibawa wannan maganar muhallin zama azuciyarki kisani Usman dinki yayi murna daganinki yakumayi farinciki Farincikinda bazai faduba kukanda nakeyi najin dadije Deejarh na kinshayardani Zuma maimatukar dimautarda hankalin mai hankali narasama mezanyi nikaina dadin dayayimun yawa shine yasakanie kuka yasassauto da murya saitin kunnenta yaradamata kinada matukar ni ima Deejarh na hakika nayi babban dace danasameki"" .wata kunyace takama khadija tashige jikinsa tana nuku nuku Dariya yayi marar sauti yace yanamai sake sakata jikinsa sannan yakirah sunanta Deejarh na "" tace na am batareda tadago fuskarta daga jikinsaba Shimadin baidamuba Yace suwaye waisuka saceki??? Dam gabanta yafadi anya karyarta zatashiga kuwa?? Gashi batasaba dayin karyaba saida tayi danjim tace wlh nimadai bansansuba Inadaki bayan kafita sallah sainaji kamar kururuwar mom awaje shine nasauko akangado dasauri nafita waje naga menene yafaru Dafitana sainaji kamar anbugamun Abu akaina" sainafadi nasume bansake sanin meke faruwaba Ashe bayan suntafi danie saisukaga kamar namutu danban farfadoba saisuka yardani cikin jeji wadansu Fulani masu yawo sukaganni dasukaga inada rai suka daukeni zuwa Dan sansaninsu Acen sukacigaba dayimun maganie harna warke saidai namanta komai sun tambayeni garinmu da sunana nacemasu banda suna dasukaga kamar namanta tunanina sukacigaba Dazama danie sunakuma banie maganie nawarke komai inayi kamar lafiyata qalau amman inada damuwa dasu da yayansu adda sukecemun taredasu nazauna hartsayin shekara biyu sai alokacin tunanina yadawo jikina Tunda nabude baki sunanka kawai naketa ambata anan ne inna wacce itace matar hardo "" tatambayeni wayekaidin nacemata mujinane """ tace ayya toyasunanki????? Nacemasu sunana khadija Todayake sudin fulanin tashine kuma damadai jinyana kawai yatsaidasu dasukaga nawarke saisuka kaini gidan wata hajiya sukace inzauna nan kafin nasakejin sauki sainakoma gida Sukatafi sukabarni dayake matar tanada kirki wajenta nazauna harna sake wartsakewa shine tabanie kudinda fulanin sukabata tabanie nadawo gida takai karshen maganar tana kallonsa Kallonta yakeyi. Cikin tausayi yace sannu Deejarh na Ashe bakyada lafiyane kullum cikin kiran sunanki nake azuciyata koda zuciyarki zataji kixo gareni Amman sainaji shiru Ninasan basu kashekiba Dan inajin haka azuciyata shiyasa nakasa fitarda raina dasake ganinki Allah shine abun godiya wlh khadija nikadai nasan halinda nashiga narashinki akusa danie kowaye yadaukeki yacutarda rayuwata hisabi tsakaninmu saigaban Allah danbazan taba yafemasaba ! Khadija tsuru 😳tayi tana kallonsa aranta tace bakasaniba ai matarkace wacce kakeso kakeganin kamar babuwata maisonka sama da itah Usman ganin takafa masa ido kuma tayi shiru sai yahurah mata iska cikin idonta take tarufe idon tana murmushi"" shima murmushin yakeyi Dan farincikin dayake cikinsa bazai faduba Ahankali taradamasa katashi muyi wanka hubbyna" kanta yadago yace dani zakiyi wankan yau tarausayarda kai tace sosaima idanma kanaso inyimaka nizan iyah Dariya yayi maidan sauti yace ainasan bazaki iyaba kodama kinyi kunya bazata barkiba tace hmm hubbyna kenan tobari kaganie mikewa tayi tasoma Jan hannunsa waizata tasheshi Amman ko motsi baiyiba sai dariya takemata wai tazama raguwa Kukan shagwaba ta azamasa nidai katashi"" yana dariya yamike yace tokar amun kuka natashi kawai yasunkuceta sukayi hanyar toilet itakuma takwantarda kanta akan faffadan kirjinsa tare sukai wanka yasake daukota suka dawo dakin"" tashirya sukayi ra ka a biyu tanuna godiyarsu ga Allah sannan suka kwanta tana makale ajikinsa" wani sanyin dadine sukeji yana ratsasu hardai Usman ganinyau komai khadija tanayimasa babatun kunya yace aransa dama idan kayi nesa damutum kukahadu jiyake kamar yacinyeka Allah yasadai Deejarh na tadaure dayin hakan yayimata addua sannan yasake janta jikinsa Babuwani jimawa barci maidadi yadaukeshi Wanda rabon dayayi irin wannan barcin tunsuna Dubai da khadija mafarkai masu dadi masu kumshe da ni ima farinciki dakuma soyayya yaukam sunkusan makara saida habu yakirashi awaya yaji kolafiya yaubaitashi dawuriba Dasalati yafarka yadauki wayar ganin habu Kuma gashi yaga lokaci yayi cemasa kawai yayi kuje ganinan zuwa yakashe wayar yasake watsa ruwa yadauro alwala yatashi khadija sannan yawuce Bayan tayi alwala tayi sallah"tana lazimie Usman yadawo saman gadon yaje yazauna tashafa addua tamike tanade abar sallar sannan takarasa akan gadon Saman jikinsa tazube tasunbaceshi akan labbansa tace morning dear"" hannunta yajawo tasake hayewa jikinsa yasagalo hannuwansa ta kugunta yarike yana kallonta yace antashi lafiya tarausayarda kai tace rasss makuwa indai annurin zuciyata yatashi lafiya"" Usman murmushin dadi yayi yace nikam ai kalaunake tunda inatare dake"" murya kasa kasa tace dagaske?? Yanda taimaganar saida tasaukarwa Usman da kasala yalumshe idonsa wadanda suka kankance yabude yanayin yanda yake kallonta kadai ya isah yagamsarda khadija yanayinda Usman yakeciki Murmushi tayi tasake matsowa tahade bakinta danashi tana tsotsa ahankali kamardai yanda taga yanayimata"" Usman saiyakara susucewa yasoma aikamata da wadansu sakonni masu rikitarwa dakuma wuyar fassarawa khadija kanta tasan Usman yahadu bashida wata makusa gashikuma ya iyah soyayya duk lokacinda suka kasance atare yakan mantarda itah komai dakowa bataganin kowa agabanta saishi Aisha✍🏼 [3/26, 8:34 PM] Nabila Elharun Q: ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠ Chapter 008 By Gentle Lady💃🏽 Tanaji aranta inama Usman natane itakadai"" sundade suna faranta ran junansu sannan suka sake komawa barci Wainikuwa nace Usman yamanta da lubabatu ne??? Hakanne kuwa wlh Sam yamanta da itah yadauka wata duniyar suke daban"" Zuwa kamar karfe takwas darabi khadija tafarka ahankali tajaye jikinta dagajikin Usman taturah masa filo ganin zaisake rungumeta Tasauko ahankali takoma daya dakin tayi wanka kaya maras nauyi tasaka tasa karamin hijab tasauko kasan bakowa hanyar kitchen tanufa tasamu kukunda yake dafa abinci yazo yana jiran lubabatu tasanar dashi abunda za agirka Saiyaga bakuwar fuska"" tashigo takalleshi tace morning"" yace morning Anty"" batareda tasake kallonsaba tasoma hada kayan da zatagirka abinci Ganin hakan yamata magana anty me za ayi yau" tadan yatsina fuska tace katafi kawai idan mom tanada bukatarka Zata nemeka yace okay yasakai yafita abunshi Khadija tasoma fire doya tadora awuta sannan tahau gyaran kayan ciki"" tacire anta daban tayankata kana na2" tadora tafasarta daban " tasamata magi da gishiri bamasu yawaba Lubabatu tanacen dakinta tunjiya dadare taketa Shafa madubin tsafinta Amman shiru babu bayanie karshe madubin yana hannunta tana kuka barci yadauketa"" garin barci tasaki Dan madubin yafado kasa yawatse"" Batasan yafadiba sai kwasar barcinta takeyi abunta"" khadija kuwa doyar tanayin taushi tasaukar da itah"" tareda antar tayi lubus"" kwai tafasa tanika tattasai da tarugu kadan ta zuba ciki sannan taxuba antar aciki""takara murzashi yadargaje tasaka kayan dandano"" sannan tadorah ferfesun kayan cikin tadan matsamasu lemun tsami kadan tazuba ruwa dakayan miya batasa kayan kamshiba tamiyar tarufe Tadorah tasar tuya tazuba mai"" dayayi zafi tarika tsoma doyar acikin ruwan kwan masu anta saita jujuyashi sannan tadibo daruwan kwan da hantar tazuba acikin tallen haka tayi hattallen yacika dayasoyu tajuya Tuni kamshi yasoma gauraye gidan"" kayan cikin bayan sun taso sau biyu sannan tazuba kayan dandano Dana kamshi"" Usman yasake juyi yasake makale filo saiyaji yalotsa ahankali yasoma lalubar filon yatabbatar shidinne yadaukeshi yawurgar yasoma lalubar khadija baijitaba zunbur yatashi zaune yasoma saurare kotana toilet ne kuma baiji saukar ruwaba mikewa yayi yawatsa ruwa 3quarter baki yasaka dakaramar Riga ja mai karamin hannu"" yataje sumar kansa yafesa turare sannan yafito sauran dakunan yasoma lekawa ganin haryanzu bata dawoba Amman bataciki"" Sauka yayi kasa tunkafin yakai yasoma shakar kwamshin girki yalumshe idonsa"" Sam baiyima tunanin agidansa kamshin yake tashiba" yasauko falon baigantaba"" sai ya tunkari kitchen din"" bakin kofar yatsaya yajingina jikin kofar yarungume hannuwa yana kallonta Batasan da zuwansaba saida kamshin turarensaa yadaki hancinta Tajuyo ido tadan turo tace badai harka tashiba"" ??? Harararta yayi cikin wasa yace aidole kice hakan""kintaso bada izininaba shine harda turamun filo ko anfadamaki jikinki daidai yake dafilo"" tace todakumafa??? Yace aijikinki yafishi taushi Dariya tayi tajuya tana motsa ferfesun tace sorry hubbyna banaso katashine bangamaba"" takowa yayi zuwa indatake yadorah kansa akan wuyanta yashaki kamshin jikinta yalumshe ido yace kimmanta yau weakened ne bazanje ko inaba"" kodama ba weakened bane banajin zan iyah fita nabarki hutuma zanyi konasati biyune inmaida jikina Dariya khadija tasamasa tace waikana nufin karame?? Ganin nawa zaisaka kamaida jikinka" murmushi yayi maidan sautiii yace sosaima kuwa aikinsan mutum yanacin abubuwan Gina jiki masudauke da vitamins calcium tyrosine dasauran abubuwanda suke gina jiki Toni kodanacisu abanzane danbasuda sinadarin Kece kawai kikeda sinadarinda duka kayan marmari basudashi danni banga amfaninsu ajikinaba Khadija tace kadai fada"" yace kuma dole ayardaba kusan taresuka sa dariya" tace kaganie kanaxuwa nasoma shiriricewa Yace bakuma zantafiba saidai mukwana anan munayi nimafa na iyah girkin nan bari kiganie "" tace kabarshi karka bata jikinka yace aiga kayan aikinan baki sakaba kema yajawo wata drawer saiga rigunan dayawa wasuma cikin ledarsu ba ataba sakawaba"" yadauko biyu yacirosu aledar yasaka daya Itama yadauramata tanacewa dama kabarshi nida nakusan gamawa"" yaharareta yace munkusan gamawa dai ina taremukai girkin nan Tace hakane kam munkusa gamawa da surutunka ba yayi dariya yace aiyau zakuci abinci maidadi tunda nasaka hannuna"" baridai inhadamana tea dannaga bakiyiba"" yayi maganar yana kunna wani gas yawanko tukunya yadorah yazuba kayan yaji daruwa da Lipton yarufe tana gefe tana kallonsa Yajuyo yakalleta yadaga mata girah yadai kallo haka waikindauka nidin ban iyah komaiba babu abunda mace zata nunamun sai Abu daya"" yayi maganar yana dariya kasa kasa tasan abunda yake nufi dariyar itama tayi tace aiho ashedai akwai abunda zamu nuna maka dasauki to Yace hakane kam bazanyi jayayya ananba" yace wainikuwa ina kukun gidan nan dakika shigo kitchen bakiga yanda momyn Abdul takeyiba"" Tace naganie tomenene ranar hannuwana idan nakasa dafawa mijina abunda zaici banason kanacin abincin kukun nan dakaina zandinga yimaka """ Kallonta yake yanasakin murmushi karasawa yayi wajenta dasauri yarike kugunta yadagata yana juyi da itah yasakar mata kiss yace ashedai nidin dan lelene bansaniba Amman naji dadi sosai shiyasa nake kara sonki Dariya tasomayimasa shima dariya yake lubabatu wacce tunda tafarka tsarabar kamshi yadaki hancinta tataso afusace dantadauka kukune yadorah abincin kuma tafadamasa karya sake yadorah girki inba ita tace ga abunda takesoba Tana kawowa kafarta taji talake ganin Usman dinta yana juyi da khadija acikin kitchen suna dariya wasu hawayene masu zafi suka saukomata gashi jiya tasha kuka fuskarta duk ta kunburah nikam nace yi aniyar hawayenki sukare Ganin kamar zasu juyo taja kafarta dakyar takoma falon tazauna tadafe kantaa"" tanajiyo dariyarsu harcikin ranta""ga takaichin madubin ta yafashe gakuma takaichin Usman da Khadija dayarufeta harsuka gama girkin suka zuba komai acikin kula sukadauko sunafirah ta soyayya suka jerah saman dinner Sam basu gama lubabatu ba khadija tagyara kitchen din Usman yana gogewa Kitchen din yayi tsaf kamar ba ayi aiki acikinsaba"" sukacire rigunan suka fito yana rike dahannunta harzasu wuce yaga lubabatu zaune tadafe kai hannun khadija yasaki yace yasalam meyake damunki yayi maganar yana zama kusa da itah yadago fuskarta ganin yanda takumbure Yace meyasamu idonki haka lubcy"??? Murmushin yake tayi tace bakomai kainane yakeyimun ciwo tunjiya" Usman yace haba lubcy shine bakisanar daniba Tasake murmusawa tace bakomai naga kanatareda Amarya kuma kundade Baku haduba banaso nakatsemaku jindadinku"" Yayi murmushi Allah sarki matata shiyasa nake kara sonki yayi maganar yana janta jikinsa "" khadija juyarda kanta tayi gefe saboda takaici Usman yalurah dahakan yamike yace bari muyi wanka kema kishirya sainakaiki asiviti Tace ah ah dama kabarshi yace kinsanfa banason musu kitashi tace to yajuya wajen khadija yanayin yanda tajuya kanta yabashi dariya saidai bayaso yadara yasakata kuka Hannunta yariko yace mujeko harararsa tayi tawuce yabita dasauri taruga tana dariya yana cinmata yadauketa yahau mataka zuwa bangarenshi Lubabatu tabisu dakallo jitakeyi kamar taje tarufesu da duka"" saida suka dade dawucewa sannan tamike tahau saman tayi wanka tashiryo hartadawo dasu fitoba tazauna jiransu gashi tanajin yunwa Ajima a jima saitakalli hanyarda zasufito tajatsakie tanajiyo dariyarsu asaman"" takai akalla mintuna goma zaune sannan suka sauko shigar shadda sukayi iri daya tunna aurensu Itama lubabatu shaddace Amman ba irinsu dayaba khadija rigarta doguwace anfitarmata da shefdin jikinta tamkar ajikinta aka kero rigar"" Suna zuba kamshi khadija tace mom sorry mundan Dade gashi bakida lafiya"" tayi yake bakomai khadija tayi maganar tana mikewa suka karasa saman dinner khadija tazuba kowa nashi itakam da Usman tahade nasu Sukasoma ci babu Wanda yasake magana harsuka gama khadija takwashe kayan "" yace tadauko mayafinta tarakasu Tace ah ah katafi nizanyi aikine"" yace tarezamu dake kibari idan mukadawo natayaki aikin"" batasom sutsaya musu tajuya tahau saman Lubabatu tace meyasa kakesoñ tilas tamata abunda batayi niyaba"" yamatso kusa da itàa yace lubabatu bakisan yanda nakejinta ajikinaba banajin dadi idan banajinta kusadanie Lubabatu tarufe idonta tabude saboda radadin maganarsa tayi danasanin tambayarsa"" shikuwa Usman baidauka wai zataji haushiba Shikam iyakar gaskiyarsa yadauka bataji komaiba har khadija tafito lubabatu tayi gaba shikuma yatsaya kallon khadija tare suka jerah koda suka kai yabude kofar gaba lubabatu tace khadija tazauna itah tazauna baya Khadija tace ah ah mom bayan nakeso kafin lubabatu tasake yin magana har khadija tabude baya tashigà Aisha✍🏼 [3/26, 8:34 PM] Nabila Elharun Q: ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠ Chapter 009 By Gentle Lady💃🏽 Usman yace kishiga to muje tarufe kofar tashiga gaba"" shikuma yazauna mazaunin drever yatada motar maigadi yabude masu kofa yana gaida Usman yace adawo lafiya Hannu yadaga masa sannan suka fita "" madubin motar yasaitashi tayanda zaidinga ganin khadija itama shitake kallo suna hada ido yasakar mata làllausan murmushi"" Kiss tayi tahura masa "" shima yamiyar mata yanamai lumshe ido cikin murmushi "" itama tamiyar masa""da martanin murmushinsa duk tsiyarda sukeyi lubabatu tana kallonsu lallai wannan yarinyar bariki kawai takoyo waima wannan khadija ce??? Yarinyarda tasanie tanada kunya sosai Amman yanzun tafitsare idanuwanta agabantama komai yitakeyi tayi kwaba ai wlh bazan zuba miki ido kinayin abunda kikaga damaba abundama mijina baiyimunba"" keyana maki yarinya kamar aljana"" Tanata sake sakenta sukuwa daga nesa suke aikawa junansu sakon soyayya harsuka kai hospital din yace khadija tajirasu amota bayaso ana kallonta"" yakunna mata Ac wayarsa takarba"" takwanta jikin kujerah tana latse latse sukuma suka wuce Kowannan maganar takona ran lubcy waibayaso ana kallonta watoga zinariya"" tanagaba yana bayanta suka karasa dakin doctor Khadija lambar wayar labila takamo tanasoma ringing akadauka da alamu barci ma take tace hello"" Khadija tasaki murmushi tace Assalamu Alaikum zunbur labila tamike tana mutsuts tsuka. Ido "" saida khadija tasake maimaita sallamar sannan labila tace muryar wanakeji kamar sahiba??? Khadija tace nice mana labila"" sai labila tafashe dakuka tace kina ina sahibata Dan Allah kifadamun Khadija tace da wayar wakikaga nakira??? Labila taciro wayar akunnenta takalla tamiyar tace wannan number dadyce ai Khadija tace to ina tare dashi"" labila tace dagaske ganinan zuwa" khadija tace dakata karatun fa??? Tace wlh bazansake kwana daya agarin nan ba kedai kawai sainazo batajirah jin mezataceba takashe wayar tahau shirin kaya"" Khadija taciro wayar ajikin kunnenta tana murmushi sannan takamo lanbar ya muktar farinciki fal ranta tasoma kiran layin harta tsinke baidagaba saida tasake kirah sannan yadauka Yakara akunnenshi tamkar Wanda bayason magana shikanshi duk yarame dankullum cikin tunanin yar kanwarsa yakeyi sallamarta dayaji tasashi mekewa cikin farinciki yace sapna kece kuwa?? Dariya takeyi tace nice Yayana kana ina??? Yace shekaranjiya nabar kano Amman ke kina ina"" tace inatare da dady cikin kaguwa yace sapna kina duniyar nan Amman kika kasa nemanmuko?? Tace Yayana kaima kasan inhar inacikin jindadi dole na nemeku saitabashi labarin yanda tasamu kanta kamar yanda tafadawa Usman yatausayawa kanwarsa sosai Yace yana nan"" tafe shima Dan yanason ganinta yagasgata lamarin tacemasa saiyazo sundanjima suna magana ganin su Usman sunfito yasa taimasa sallama Taresuka kawo bakin motar yabudemata tashiga shima yazagaya mazauninsa yana kallon khadija yace dawa dawa kika Kira?? Tace kai hubbyna bafa waya nayiba"" yanda tayi maganar kamar wata Yar yaye yabawa Usman dariya lubabatu kuwa guntun tsaki taja Wanda babu Wanda yaji sai itah datayi abunta Yace ainasan wayakikai tunda naga fara a tayawaita afuskarki "" tarausayarda kai tace ya muktar kawaifa nakirah sai sahiba Yace dama ainasani" tace kumafa tace tana nan zuwa yau zatashigo jirgi"" yace haba aidole ainasan itama tayi kewarki Nisam namanta ko hajiya bansanarwa dawowarkiba inacikin zumudi Yayi maganar yana kanne mata ido daya motar yakunna suka hau hanya wajenda ake siyarda maganie Yasiya mata maganie suka wuce gida"" yanayin pkng khadija tafito tayi cikin gida saida yafito yabudewa lubabatu suka wuce tare yana mata magana Dan Allah maman Abdul kicire damuwar aranki tunda gashi tadawo aikomai yawuce ko"" Tace hakane aibakaji dadin danajiba wlh murmushi yayi yace bakikainiba ai daidai sunashiga gidan harsama yarakata yadibomata ruwa tasha maganie sannan yakwantarda itah yanabata labari harbarci yadauketa sannan yajaye jikinsa daga nata yajamata kofar yafita Bangaren khadija yanufa yashiga yanakarewa dakin kallo waidaga zuwansu hartashiga tayi gyaran daki ko ina yayi fes yana zuba kamshi Tana bandaki tanawanka saboda yanayin zafine tafito daure da towel"' tana goge jikinta tacee harkafito?? Yace ah sarkin aiki harkinyi garanki bayankuma nace kijirah natayaki" Tace nahutardakai kwanta kahuta"" rigar jikinsa yacire yace saimunyi wanka" tace saidai kayi wanka aini nayinawa towel yadaura kawai yasunkuceta yayi toilet yana cewa ban yarda dawan nan wankanba aiwayo kikamun Bayan kibari sainazo muyi tare tana dariya tahau zillewa tacee kasaukardani to"yace abahon wankaba zatasake magana yahade bakinsu waje daya Tanata hum hum hum bahalin magana tafito sai cikin bahon wanka yasakata har towel din" Yatara ruwa shima yashiga tasha mur wai itah tayi zuciya yakura mata ido ruwan yadibo yawatsamata afuska ta kyalkyace da dariya tadibo itama tawatsa masa saisuka koma wasar ruwa sundade kafin suyi wanka sannan suka fito basu Shafa komaiba suka kwanta suna makale dajuna barci yadaukesu Sai kusan karfe biyu suka farka khadijace tafara tashi saida taje tadora abinci sannan tatasheshi yayi sallah ita ma tayi suka je kitchen din tare dama jelof din shinkafa tadora danganin sun makara Tace wainikuwa meyake damun mom??? Cikin alamun tausayawa yace mata jinintane yahau saboda tunani Tace tunanin lafiya hubbyna metanema tarasa?? Yace kemana tunanin batankine yasakata adamuwa"" khadija tace ko??🤔 Yakalleta bangane koba bakiyarda bane?? Tace nayarda mana aibansan harhaka takesonaba yace toyanzu kinsani ai tace Allah sarki itakuma tata kalar soyayyarce tazodahaka"" 🤔 Usman dabaisan dawon garinba yace aikuwa nitausayima takebani wlh kinga yanda tadamu lokacinda kika bata kullum cikin kuka take Khadija tamere baki kawai saida abincin yanuna takwashe tahadamasu lemun kwakwa"" sannan suka jera kayan yatafi tashin lubabatu danyasan batafarkaba. Khadija kam wani wankan tasake fesawa tasaka kananun kaya tana fesa turare Usman yashigo yace tundazufa muke zaune kekadai muke baikarasaba sauran maganar ta makale abakinsa yace wow Masha Allah kinganki kuwa"" yakaraso inda take dasauri"" "" tagama nade gashinta tace tomuje"" jawota yayi yana shinshina yace muje ina kibari nabiya kudin kwalliyar nan mana"" Tace ah ah nayafe yanzunfa kace kunajirana da mom zataga mun Dade ai"" tayi maganar tana jaye jikinta daga nashi Yace haba Deejarh. Yanzun rowa zakimun inaji inaganie??? Tarausayarda kai tace kasan bansababa Amman ai yakamata kaji uxurina akwai anjima aiko Yatsuke fuska ainasan da anjimar nifa baburuwana datana jiranmu barito nacemata taci nata "" ta gwalo ido tace kukuma kuyi mene??? Yace karatu kawai zankaramaki saimuje muci ko"" Tace nagode dawan nan bitar dannituni nahardace komai kazo mutafi Dan Allah kamin ranta yasosu"" hannunta yariko yace haryanzu baki fuskancetaba nasan bazataji komaiba Deejarh Takalleshi da mamaki tace hakane dayake itadin batada kishi toni yunwa nakeji Tanakai karshen maganar tajaye hannunta daga jikinsa tafita aranta tanacewa bakasan damuwar matarkaba dai Usman bakisake yake kallonta yagirgiza kai sannan yafita koda yaje harsun soma cin abinci dagayya yasaka chokalinsa cikin abincin lubabatu yanaci waishima saiya sosawa khadija zuciya kamar yanda tasosa masa Illai kuwa khadija taji haushi Amman tagano yayihakanne dagayya saikawai tashareshi" tacigaba dacin abincinta tamadaina kallonsu Lubabatu kam ganin hakan saitasoma Jan Usman dafirah shima yabiyemata" khadija kam tamiyarda hankalinta wajen cin abincinta Saida takoshi tamike tadauke plate dinda tabata takai kitchen tafito tayi hanyar dakinta"" Usman tagefen ido yake kallonta sai hadiyar yawu yakeyi Lubabatu talurah dahakan aranta tace nimafa Na iyah barikancin nan yarinya idan kinsan wata bakisan wataba indai dawadan nan kayan kike rudar Usman nima zandinga sakasu inga karyar bariki Tsaki taja Wanda yasaka Usman juyowa dangabadaya yakarkata kansa wajenta. Damamaki yace lafiya menene yasakaki yin tsaki??? . Waiyau wace rana lubabatu takasa boye kishinta" kamar jirah take ya tambayeta saikawai tafashe dakuka yace yasalam menenekuma Dan Allah karki tayarmun dahankali yajata jikinsa yana rarrashinta Yace me akaimaki matata Dan Allah kidaina kukan nan yana konamun zuciya"" cikin kuka tace yanzun kadaina so nane ko??? cikin sauri yace wayafadamaki akwai ranarda usman zaidaina sonki??? Aiduk wacce zanso bayanki take"" lubabatu dankenafara sokamin wata"" Amman meyasa kikace haka??? Nayimaki wani abunne dabakiso??? Kifadamun banason nacutardake koda cikin rashin sanine Aisha✍🏼 [3/26, 8:34 PM] Nabila Elharun Q: ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠ Chapter 010 By Gentle Lady💃🏽 Taja nunfashi tace neyasa kakeyimun haka nalurah tunsanda yarinyar nan tadawo gabadaya hankalinka yakarkata zuwa gareta menene kakeso ajikinta Wanda nibanidashi . Dankawai kanaganin ina kauda kaina bashizaisa komai kanayi agabanaba nimafa inasonka kuma dole inyi kishinka tunda nima macece"" takai karshen maganar tanasake fashewa dakuka nikam nace takarewa lubcy🙅🏻 tundahar tafurtawa Usman tana kishinsa Sosai yaji tausayinta lallai kuwa tayi hakuri sosai yace kiyi hakuri bansan abun nan zaibata maki raiba aidabazan yiba Amman zankiyaye bazan boyemakiba lubcy Wlh duk sanda khadija tabar inda nake jinakeyi kamar tareda zuciyata tatafi gabadaya zanrasa natsuwata sainajita akusa danie Amman nibabu abunda takedashi Wanda bakidashi"" aransa kuwa yace akwai abubuwa dayawa Amman bazaiso ranta yasosuba yanda itama tanuna masa halacci aiyadace yayi mata" sosai yaso yaje wajen Deejarh danfa soyake yabiya kudin kwalliyar nan Amman yanajin nauyin tashi badan ransa yasoba" yazauna suna taba fira saida akai la asar yatashi yayi alwala"" dakin khadija yawuce yaturah kofar yajita arufe yagirgiza kai kawai yafita zuwa masallaci Khadija kuwa tun lokacinda tabarsu takoma dakinta tarufe kofa takwanta tunanine falranta sosai tanason boye kishinta badan komaiba tasan muddin lubabatu talurah tanada kishi zatayi amfanie tawannan hanyar danta muzguna mata Amman duk yanda taso taboye kishinta akan Usman takasa tana kwance wani barcin yadauketa Sai lokacinda Usman yaturah kofa sannan tafarka tayi sallah tasauka kasa tadorah girkin dare"" lokacinda Usman yadawo sallah yanajin motsi kitchen yasan khadijace kaitsaye yanufaci kitchen din dama kofar bude take Tabakuma kofar baya tana yankan alayyahu"" saman drawer din yahau yaxauna yana kallonta"" uffan batace masaba tacigaba da abunda takeyi"" shima baicekomaiba saidai binta dayake dakallo yana murmushi" bayan tagama dorah ruwan tuwon tazuba shinkafa tahada komai namiya tawanke hannunta tafita abunta nan tabarshi zaune Mikewa yayi yabi bayanta"" tanaganin hakan tasoma sauri taresuka kai kofar dakin taturo kofar zata rufe yatura da daya hannunsa saiga khadija tayi baya zatafadi yatarota dahannu daya" tajuyo daniyar magana suka kurawa juna ido Hancinta yaja yace bakida karfi meyakaiki rufe kofa"" murguda masa baki tayi tace narufe din nika kyaleni"" tayi maganar tana tashi daga jikinsa shikuma yaki sakinta yaja ta sai kuryan dakin damadai yace saiya biya kudin kwalliyar tuni khadija tamanta dakomai sukacigaba da soyewarsu ******************** Karfe goma jirgin su labila yasauka Dan adaidaita tahau zuwa gidan yana sauketa tabashi kudi dasauri taja kayanta tashige gidan tana kwalawa khadija Kira Khadija tamike tsaye cikin fara a dagudu suka rungume juna saisuka fashe dakuka Usman da lubabatu suna kallonsu Usman tausayi sukabashi itakuma lubabatu haushi sukabata saima tadauke kanta daga garesu"" Sundade suna kuka akarasa Wanda zai lallashi wani khadija ce tasoma rarrashin labila ganin takidaina kukan tamike taja hannunta sukahau sama"" saman kujerah tajata suka zauna Khadija tace kidaina kukan nan Kawata komaifa yawuce tunda gani nadawo ban mutuba"" labila tashare hawaye tace Amman suwaye suka daukemunke?? Khadija tace Allah masanie kinjidai yanda nasamu kaina tabata labari kamardai yanda tafadawa Usman Labila tace shegu sosukai rubani dake Allah yafisu wlh banyafemasuba dansun cutarda zuciyata"" khadija ta ce hardake hakan zakice to hubbyna yarigaki.. Labila takwashe da dariya tace habadai yaushe kikahau hanya"" 🤔khadija tace zauna nan ainiyanzu saidai inkoyardake"" 😉 saiyanzu labila taga kayanjikin khadija tamikarda itah tasoma kallonta sama dakasa takwashe da dariya tace kinyimun daidai banmusha 💁🏻suka taba.. Usman sunajiyo dariyarsu kamar al mara"" labila tace Amman waye yaciremaki wannan kunyar??? Khadija tayi fari da ido tace hubbyna mana keya karatun??? .. Labila taja hannunta suka zauna tace bawani dadi wlh sahiba inacikin matsala" khadija tace matsalar mene sahiba??? Tace hmm tunani mana bakiga yanda na lalaceba shekarata biyufa acen Amman duk akai jarabawa sainafadi danbana iyah rubuta komai.. . Damuwa tayimun yawa kema kinsan bamatare hankalina bazai kwantaba tundanaje bandawoba saibikiñ uncle hafis Khadija tace waikina nufin yayi aure??? Labila tace sosai kokina nufin bai isah ba aini naga yadadema baiyi aureba"" Khadija tace nibance yayi sauriba nasodai ina nan akai bikin inason zuwa kano wlh Labila tace tosaibiki kishirya gobe mutafi saidagacen ma kiga matar"" kusa da layin mu gidansa yake babuwani nisa Khadija tace kinaganin hubbyna zaibarni natafi nimafa banason inyi nesa dashi"" labila tayi dariya tace keyar nan yaushe kikazare har haka??? Tayi farr da ido tace ran talata sukasake darawa tace bari nadebomaki abinci yaufa akwai labari labila tace mujeto tare suka sake fitowa labila taradamata akunne tace kinja kayafa wlh bakiga yanda kike tafiyaba har magana suke aidole kiruda babana daidai suna saukowa "" Khadija tace Abu dole yakika ganie tayi maganar tanawata tafiya maidaukar hankali labila tasaki baki tana kallonta Usman shima baki bude yake kallonta labila tace wow wlh kina burgeni sahiba suka tafa atare suna dariya khadija taja hannun labila dasauri suka shiga kitchen tarufe bakinta tace ke wlh Sam namanta hubby yana falon nan nayi wannan tafiyar Labila tace toshine me ni wlh bakiji yanda kika burgeniba gabadaya kintafi da imaninsa kinayifa aini hakan nakeso tawan Khadija tace nifa mom nakeji aisaita daukeni marar kunya labila tace saime ina agidanki kikeyi bawajeba kinga wlh danice nasamu wadan nan mazaunan sake turosu zanyi"" haka zanrika tafiya labila tasoma tafiya tana murguda duwawu khadija mezatayi inba dariyaba "" sosai tabata dariya itah batada duwawun Amman tadaddage taturosu Khadija tace baridai mukoma daki kinji tazuba abincin tadauka suka fita labila tace dansakeyin tafiyar mana"" harara tamaka mata tace bazanyiba Sukawucesu tamkar basu gansuba" dakima sai surutu suke har labila tagama cin abinci tawatsa ruwa tace sahiba rakanie inje inkwanta nasan kinmatsu kije wajensa"" Tace waima nifa yau tarezamu kwanta shiyaje wajen mom"" labila tace wlh baki isah ba baban nawa zakijawa ajie dolefa kitashi yarinya kitafii Taja hannunta jeki kiyi wanka inrakaki dakinsa"" ganin khadija tatoge labila tatasa keyarta saida tashiga wanka tadawo tafitomata dakayan barci masu sharara taciromata after dress Tafeshesu da turare Khadija tana fitowa labila tace kiyi saurifa kishirya gashi har shabiyu dakwata"" tayi maganar tanafita Khadija tabita dakallo kawai tashirya bawata kwalliya tayi maiyawaba yar simple ce tasaka kayan barcin"" tadauko sweet dinta tasaka abaki sannan tadorah after dress din Asama takalma masu tsini tasaka tasake feshe jikinta da tirare tafito labila tace haba kokefa kinga yanda kike daukar ido kuwa "" muje wlh nikaina barci nakeji tayi maganar tanajan hannun khadija suka sauka zuwa hawa na biyu Bakin kofar tabarta tace asha soyayya lafiya sahiba saida safe tawuce tana dariya bangaren lubabatu tanufa" Khadija taturah kofar da sallama Usman yana zaune saman kujera yana danne danne dantun kokacinda su labila sukahau saman yaji duk bayawani sakewa yanagudun kar khadija tace tareda labila zata kwana basuwani jimaba yayiwa lubabatu saida safe danyanada aikinda zaiyi Saida yayi wanka yayi shirin kwanciya yadawo falo yazauna yana danne danne ga laptop"" Amman gabadaya hankalinsa yana wajen khadija jiyakeyi kamar yatashi yaje dakin Amman bazai iyah ba labila yakejima kunya Yana cikin sake saken yaji takun takalmanta saida yasaukarda ajiyar zuciya"" yacigaba da abunda yakeyi saida tayi sallama saubiyu sannan ya amsa batareda yadagoba"" tsayinta tayi bayan tarufe kofar"" Bayan kamar mintuna biyar baiji takarasoba saiyadago yakalleta itakuma saita dauke kanta takama hanyar dakinsa tacire after dress din tafiya take maidaukar hankali dajan ra ayin maikallo tuni Usman yakulle laptop yabi bayanta"" Bayani yasha banban korafinda Usman yaso yayi natabarshi shidaya tuni yamanta dashi"" bayan sunyi wanka suka kwanta asuba tagariiii *********************** Washe gari da labila suka hada abun break bayan sungama sukai wanka sunacin abincin labila tacewa Usman dady kano zamuje da sahiba taga matar uncle tunda batanan akai bikin"" Yakurba tea yana kallonta yace zaki koyamata yawoba shekaranjiya daga dawowarta" " tace kai dady itafa tacemun tanason ganinsu malam kumafa ya muktar shima yazo shine nacemata tabari saimuje tare" Yallalli agogon hannunsa yace shikenan kushirya saimuje tare nima inason ganin hajiya akwai maganarda zamuyi Amman dakuzandawo bazaku kwana acenba" Tace haba dad"😩 khadijace ta zungureta ta waigo takyapta mata ido alamar tayi shiru tace shikenan dad zamudawo taren" Aisha✍🏼 [3/26, 8:34 PM] Nabila Elharun Q: ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠ Chapter 011 By Gentle Lady💃🏽 Lubabatu dai batace masu cikankuba "" harsuka gama cin abinci suka shirya Usman yace idan tanazuwa tataso suje tace ah ah sutafi kawai tana gaidasu haka sukafita labila tazauna baya sukuma suna gaba sunafara tafiya tadauki wayarsa takirah ya muktar tace gasu ahanyar kano dankar susha banban"" yace yanzun kuwa yake shirin fitowa barito yajirasu taka she wayar ta ajemasa Basujima dafara tafiyaba khadija tasoma hamma alamun barci takeji hartasoma gyangwadi "" jawota yayi takwanta akan cinyarsa"" tacigaba da barcinta Harsuka kai kano batasaniba kofar gidansu khadija dad ya tsaida motarsa sai lokacin tafarkà muktar kuwa yana bakin kofar suna tsayawa khadija tafito dagudu tafada jikinsa suna dariya yace sapna waisai yaushe zakisan kingirma Daidai Usman yana kawowa yace bana tsammanin yanzun saidai inta haihu"" muktar yace hakane dad khadija kam dariyama suka bata basusan tadade dahaihuwaba "" yaduka yagaidashi Usman yamika masa hannu suka gaisa Yayimasa yahanya"" yace alhamdulillah nan sukaiwa juna barka da dawowar khadija usman yace shizaiwuce wajen hajiya susameshi cen Yashiga motarsa yaja labila tana tsaye saida khadija tawaigo tace mekikeyi anan kuma sahiba tace bakomai takaraso tace ina kwana ya muktar yace kalau yagidan Tace lafiya atakaice "" takalli khadija tace barinawuce gida kigaida inna"" khadija tace yahaka bazakishiga bane nifa banason fi ili"" Labila tace nidai sako nabaki malama saikinzo"" tayimata gwalo tawuce abunta muktar yabita dakallo kasa kasa shima yadauke kansa wani gefen Na zuciyarshi yanamasa radadi Saiyaushe zai sanarda labila sirrin zuciyarshi .. ??? Sam batadamu dashiba tana nuna halin ko inkula duk lokacinda zasuhadu shikuma maganar nauyitakemasa bayaso yafurta sirrin zuciyarshi dagakarshe tace batasonshi"" Gauran nunfashi yaja yace Allah kasa labila tasoni koyayane taji abunda nakeji"" Khadija tace yadai Yayana??? Baki yadan tabe yace bakomai mushiga dagaciki kafin tasakeyin magana haryawuce tabi bayanshi Gidan cike yake tamkar anabiki gwaggo hassana da Husaina dayaransu sulaiman dahiru duk sunagidan yauko malam. Baifita kasuwaba"" jin khadija zatazo dama tunda muktar yadawo yasanardasu sapna tadawo Zokuga murna kamar zasu hadiyeta sai nan nan akeyi da ita muktar gefedaya yakoma yana sauraren firarsu Amman zahirin gaskiya tunaninsa baya wajen Tunaninsa yanawajen miskilarsa sunanda yasaka mata kenan awayarsa saikayan number dinta yakeyi yakan kirah idan tadauka sallama kawai yakeyi yayi shiru tayita magana yana sauraren muryanta saitagaji taja tsaki takashe wayar Kuma itama takasa goge number awayarta duk da Batasan Wanda yake kiranba" amman muryansa tanayimata dadi sosai "" miskili itama hakan tasaka awayarta sosai tasaba duk ranarda baikiraba saitajita wani iri Tana kokarin cireshi aranta danbataso tasaba alqawarinda tadaukarwa sahiba cewa kowannensu shizai zabawa Dan uwansa miji Sam hankalin muktar yabar jikinsa tunowa yayi datsiwarta yayi murmushi Su khadija sundauka yana biye dasune basusan yatafi wata duniyarba sundade suna firah muktar yadauko mata wayarta dazata tafi gidan hajiya taresuka fita suna tafiya tacemasa ya nikam intambayeka Kallonta yayi yace inajinki"" tace kataba zuwa Niger wajen dangin mama??? Yace ah ah meyafu ??? Tace kawai inason zuwane" murmushi yayi yace aganinki zasu kalleki kitunafa mahaifiyarmu ma batasamu kallon arzikiba" Khadija tace nasani Amman insha Allah inada burin zuwa" yace shikenan nidai bazan hanakiba idan mijinki yayarda kije daidai sunkai kofar gidan tace yaushe zaka komane??? Yashafo sajensa yace gobe zankoma aiki yanajirana wlh haka nadauki Hutu dannazo naganki dayake banine kawai mai duty ba Tace shikenan aitunda gawaya zamurika waya akai akai"" yace shikenan sundan jima suna firah tace bari tashiga yace to yajuya itah kuma tashiga gidan Cikin falon tasamu hafis da Usman da hajiya suna firah tagaidasu sannan tamike tashige dakin labila Kwance tasameta tana kallon silin da alamu tunani takeyi duka khadija ta danamata acinya saida tasa kara tamike"" zatayi magana kenan wayarta tasoma ringing takalli khadija takalli wayar Khadija tace me nakallona kidauka mana"" labila tadauka takara akunnenta" Muryansa maikashe mata zuciya taji taratsa dodon kunnenta "" amincin Allah yatabbata agareki annurin zuciyata"" wani dadine yaratsa zuciyarta talumshe ido tabude tace taredame magana"" Ajiyar zuciya yasaukar mainauyi"" daganan shiru yabiyo baya"" takatsemasa tunani dacewa dan Allah wayekai??? Kuma meyasa kake damuna dakirah duk sanda kakirah bakayin magana komadai kai mugune aniyarka tabika tana kaiwa karshen maganar taja tsaki takatse kiran "" Khadija tayimata kuru dayan idanuwa tana kallonta"" tace sahiba"" waima waye yake kiranki inadai ba saurayi kikai a skull dinkuba dankinsan wlh nayimaki miji tuntunie Tayi chilli dawayar tace kishare banmantaba sahiba aike shaidace banakula kowa wannan dinma wlh bansan kowayeba yakedamuna dakirah Kuma kodanadauka iyakarsa sallama bayaga hakan bazaisake cewa komaiba"" Khadija tace dama yadaina wahalda kansa danni nagama zabamaki miji"" tayi maganar tana kwanciya Batajima dakwanciyaba barci yadauketa labila tanata zubamata surutu Batasan tayi barciba"" saikusan la asar labila tatasheta sukaci abinci Sanñan sukaje gidàn uncle hafis matarsà Hafsat tanada fara a gasoñ mutañe sundade sunafirà sannan sukàmatà sallama sukafito Khadija takoma tayiwa su innah sallama harbakin mota muktar yarakata badan komaiba dankawai yasake ganin labila Amman tunda tagansu tare tayi saurin shigewa motar yayiwa Usman sallama sukawuce yana kallon su harsaida yadaina ganin motarsu labila tana kallonsa tajikin madubinda yake gaba nakusa da khadija Ranar kam Usman tareda lubabatu yakwana"" washe gari tasaka kuku yashiryamasu girki Sam Usman baiwanici dayawaba dankwana biyun nan khadija tabatashi dagirkinta hakadai yake daurewa yanaci ************ Bayan watanni hudu abubuwa sunfaru dayawa lubabatu duk ta lalace khadija kuwa tatika kiba Sam batahankalto cikine da itah ba batawani laulayi kamar dai cikinsu hassan .Usman ne dayaga yawan barcinta yayi yawa gaci kamar gara yamatsamata saida sukaje asiviti ana aunata akace tanada juna biyu nawata hudu zokuga murna kamar Usman yalasheta ranar kowa saida yasamu labarin khadija tanada ciki"" Kulawa babu irin wacce batasamu daga bangaren Usman labila batabarin tayi komai yanada wata bakwai cikinta yayigirma sosai kamar gobene zatahaihu " tafiyama dakyar takeyinta cikin khadija yana wata Tara tatashi da nakuda Usman yadauketa hankali atashe suka garzaya hospital batawani dadeba tahaifo yaranta uku daya namiji biyu mata"" wayyo dadi Usman dadi duk yakumeshi lubabatu tunda tasamu labari tace shikenan khadija takwace gidan saiyanzu takedana sanin mahaifarta da akacire Daga asiviti gida akawuce da itah tundasukam amatsayin haihuwar fari suka dauka"' labila ta tattara kayanta takoma gidan hajiya Usman makusan kullum yana hanyar kano'' "" alokacin lubabatu tayanke shawarar zuwa taraba Amman bata sanarda Usman ba dantasan cewa zaiyi watasani acen"" cemasa tayi zataje gidansu sajida" tunsafe yana fita dama tayi biza jirgin karfen bakwai tabi danbataso takwana acen Amman takasa gane ainahin dajinda yake dankomai yasauya agarin rabonta da dajin anfi shekara ashirin"" haka takarace yawonta tashigo jirgi tadawo gida raibace dankuwa tayi bakinciki kuma batason tatambayi su sajida bataso suyimata dariya Dan basusan tanazuwa wajensaba haryanzu Cika bakinta duk yazama nabanza kenan Aganinsu tahanya suka haduda Usman bawai wajen boka tatafiba sukam basuje wajen bokaba dansamun mijin aure saidai dasuka yi auren sun karbo Na mallaka dakuma wanda baida ikon yimasu kishiya iyah nan suka tsaya Amman kullum idan suna tareda lubcy cemasu takeyi itah Usman natane mezaisama tawahalda kanta zuwa wajen boka domin tasa amallakeshi sukan jinjina mata toyanzu idan har tatambayesu Sunsamu abun dariya ranar Usman kano yakwana bagidaba"" Dan saurah kwana biyu suna""washe gari lubabatu itama tashirya tatafi tunda tunranarda akatafi da khadijar bata komaba Tahada kayan jarirai kala arbain duka amatsayin tata gudunmuwa"" saiyabonta akeyi gawanda baisan halintaba Amman labila da khadija ahankade suke kallonta"" Sai dare tabaro kano takoma kaduna"" ana gobe suna muktar yazo kayanshi kawai ya aje yayi dakin inna inda khadija tace bakinsa har kunne waiyanzu kanwarsa tahaihu kuma har Yaya uku"" Labila tana rike da macen khadija tana zaune biyun suna akan gado muktar yayi sallama idonsa sai akan labila wani sanyin dadine yaratsashi yakasa dauke idonsa akanta!" Tare suka amsa masa sallamar wa alaikumus salam""" gefen gadon yazauna saiyanzu labila tadago suna hada ido tadauke kanta tace sannu dazuwa ya mukty"" Yace yauwa "" yagidan tace qalau tamike ta aje jaririyar tace sahiba bari naje gida anjima zandawo"" khadija tabata fuska tace haba kinsanfa magana mukeyi gashi gobe suna bamu tanadi komaiba Tace sahiba komai dazaki bukata bazaiyi wuyaba idan naje gidan yanzun zankirah dad infadamasa sai asiyo bajima zanyiba ai zandawo Khadija tace dan Allah kizauna sahiba nifa banason kitafi "" harararta tayi cikin wasa tace inakekike da kafafuwana toyunwa nakeji aikyabari incika cikina Khadija tace yanzunfa inna takawo abinci kikace kinkoshi kedai kinsan abunda kikewa gudu labila tace toyanzu naji yunwar barimadai naje na karbomana dinki Tanakaiwa karshen maganar tajuya tafita muktar yabita dakallo"" ransa yana sosuwa shibaisan meyasa duk lokacinda yashigo yasamesu tare saitatashi Wata zuciya tace kaine batason ganie" yayi saurin kawarda zancen dankarma yasamu muhalli azuciyarsa Aisha✍🏼 [3/26, 8:35 PM] Nabila Elharun Q: ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠ Chapter 012 By Gentle Lady💃🏽 Khadija takalleshi tace yadai ya muktar"? Yanisa bakomai Kanwata yayi maganar yana Daukar hassan yace sannu sapna kinyi kokarifa haryara uku Murmushi kawai tayi sannan tace kaga kyautar da Allah yabamu mamana zata samu takwara saimukirah ta sapna tunda naga kanason sunan nan Kamar kinsanie dannima idan nayi aure yata tafari sunanki zansaka mata sainakirata sapna Khadija tace sunan baiyi yawaba murmushi yayi yace kokadan ""ya aje hassan yace to acikin wadan nan wacece babba??? Dariya yabawa khadija tace nima bansaniba katambayi dady"" kada kansa kawai yayi yace zangane dakaina"" tatambayeshi ya aiki yace Alhamdulillah " sukaci gaba da firarsu Labila batasake dawowa gidan ba saidare tashigo dakayan dinkin su gwaggwo hasana sunata hadin miyar buki tayi masu sannu da aiki sukace yauwa tashiga dakin khadija tasameta tanacin tuwo kusa da itah tazauna tazube kayan hannunta Khadija tace saiyanzu kikadawo"" hannuwa tayarfar tace wlh bakisan yanda mukai da telan nan ba saida nayimasa rashin mutunci kinga rigunanda yamana?? Aisaida nasaka yabudesu natsani insa Riga inji tamatsemun jiki waishi zamanie saiyabari sainayi aure yayimun irinsu idan mijina yanaso koni banason Dan kwalliyar gida zansaka masa Khadija tace gwadamun naganie nidai banason katuwar Riga inyita rawa acikinta Yar daidai nakeso" labila tabude tasoma nuna mata"" Ba laifi sunyi kyau"" labila tace gasunan dai kigwada idan basuyiba tunda safe inmiyar nikwanciya zanyi barci nakeji wlh "" tadauke su husaini tamiyardasu akan gadonsu takwanta babu jimawa barci yadauketa"" Innace tashigo da sallama khadija ta amsà tace tataso kawunta yana kiranta"" tatashi tabi bayan innah batajima da fitaba muktar yashigo dakin baigantaba harzai fita yahango tauraruwarsa tana barci ido yakuramata bayako kyaftawa"" tana barci tamkar tana murmushi takowa yayi kusa da itah yazauna"" wani dadi yakeji aransa motsinda yajine alamar za ashigo yasaka yatashi dasauri Yakoma wajen gadon su hassan khadija ce tashigo tace ah Yaya yaushe kashigo?? Yace yanzun nashigo bangankiba"" tace dama kayan barkane inna takiranie inganie"" yace ainagansu dazu Amman khadija kiyimasa magana yadaina kashe kudi haka ai abun yayi yawa Tace toyazanyi najima kawu yayimasa magana aini naga kokayanda mom takawoma sun isah" yace Hakane samun wuri yayi yazauna sunafirah yana satar kallon labila sai shabiyu saurah yayimata saida safe yayi dakinsa Yaukam yayi barcinsa cike da soyayyar labila dazaran yarufe idonsa itah kawai yake ganie **************** Washe gari suna hassan yaci sunan mahaifin Usman Adam anakiransa anwar sai Husaina fateema anakiranta sapna" saita ukun binta sunan hajiyar Usman anakiranta husna"" Biki kam yayi biki maijego saishiga dafita takeyi su labila kam ba a magana duk da batawani sakewa Dan duk inda tawurga saitaga ya mukty"" Bangaren lubabatu kam batayi taron komaiba"" kamarma ba abiki danbata gayyaci kowaba kawayenta mabasusan da haihuwarba Kwance take tunsafe "" taji kamar ana sallama tamike daga kwancen tana Jan tsaki tasauko kasa wacce taganie ce yasaka tasaki fara a tace wanake ganie kamar khairat??? Itama dariya take tace nice mana"" kinga nasakene Lubabatu tace karaso saman mana"" wacce akakirah da khairat tahau na urar zuwa sama sukashiga falon lubabatu"" Khairat Kawar lubabatuce unguwarsu daya a Lagos tariga lubabatu aure haihuwarta daya tunda tayi aure suka tare india batasake zuwaba saibayan lubabatu tayi aure Kuma tadaxo gidan taretake da mijinta basuwani jimaba suka tafi yanzun tsayin shekara biyu kenan da dawowarsu katsina dazama Dan mijinta Dan katsina ne"" lubabatu takawomata ruwa tazuba mata tace ya hanya"" khairat tace alhamdulillah nazo wajen wani bukine nace bari nabiyo mundade bamu haduba kinsan bancika zama kasarba Lubabatu tace hakane ina kikabar anisa?? Tace tana America wajen karatu kwanan nan takeshirin dawowa "" " lubabatu tace su aneesa anzama yanmata ni aikonaganta baxan ganetaba Tace gaskiya kam rabonki da itah tuntana Yar shekara daya yanzun aitasake kamannin mahaifinta "" duk sunfito ina labila da Abdul"? Lubabatu tamere baki tace Suna kano kinsan yaune sunan matar babansu"" khairat tace banganeba waikina nufin maigidanki yayi aure harkuma matar tahaihu??? Lubabatu tace ah yara uku tahaifa mace biyu namiji daya"" khairat takalleta sororo tace kuma kike kwance kinashan iskan fanka??? Anya lubabatu kedince danasani?? Kinfini tsiya dakomai Amman harkika bari mijinki yayi aure hartasamu gindin zama tahaihu?? Kinbata wayonki wlh Nantake idanuwan lubabatu suka kawo.ruwa maison kukane akajefeshi dakashin awaki antonowa lubabatu inda yakeyi mata kaikayi"" khairat tace waikina nufin kuka zakiyiwa kishiya??? Aibakiga komaiba wlh gashi yanzun kintsufa mijinki yasamu yarinya danya sakaf kekuma zaizubaki kwandon shara mekika tsayayi Kawata baki kada yarbanzaba?? Kodayake nasan kedin bakyazuwa wajen boka Lubabatu tace haba kawata kalleni kiga yanda na lalace kema kinsan duk abunda kikaga yasakani nayi sanyi yafi Karfina Tatari numfashinta tace banganeba akwai abunda zaigagari boka Kuwa saidai idan bakizube kudiba"" tashare hawaye tace Kawata kudin ayanzu sunkasa yimun rana yarinyar batajin maganie kuma wlh takaimun intaha harsawa nayi akasheta Amman daga karshe saikuma tadawo yanda kikasan aljannune sukayi rainonta Khaitar tace bagaskiya bane gunwanne bokan kikaje??? Lubabatu Tanisa tace sunansa *hatsabibin boka* taraba yake kuma shi ka idarsa inhar kafara aiki dashi bazaka sake zuwa wajen wani bokan ba naje dajinda yake nakasa gane wurin Khairat tace aiwannan zancen banzane"" dakudinka harsai anyimaka yanga saikace shine Kadai boka tobari kiji inada wani boka danake zuwa wajensa aikinsa kuwa shayanzu maganie yanzu take yanke bukatarki zatabiya ammanfa saikinzube masa shegun Akan kudikuwa wlh bashida mutunci danmuddin yayimaki aiki baki bashi cikon kudinsaba zaijuye aikin zuwa gareki Amman nasan kedin baza asamu matsala taban garenkiba dankinadasu Lubabatu tayi shiru daga bisanie tace nifa tsoron sharrin *hatsabibin boka* nakeyi wlh bashida imani zai iyah kasheni muddin na je wajen wani bokan"" tace kimanta dawani *hatsabibin boka* tunda yakasa kisake wani indai zakiji shawarata nidanake hulda da bokaye Kusan biyar duk Wanda yamun aiki baiyiba wani zansake Abu dakudinka harsaikayi yanga Kamar kinshiga kasuwane kowa yabaje hajarsa aiwacce kikeso zakisiya ko anamaki Dole" kinga kawai kisaka rana kisameni katsina nakaiki wajensa nibanason naga Wanda nakeso yashiga damuwa Lubabatu kam tanajin tsoron *hatsabibin boka* kuma tanason akawarda khadija khairat tace mekikace??? Lubabatu tace to to shikenan saikibanie address din gidanki dazaran angama komai zansameki saiki kainie tunda kinga yanzun bakowa gidan idan nafita za a iyah zargina Khairat tasaki fara a tace yauwa yargari kokefa saina ganki takai karshen maganar tanadauko ruwa Tasha"" tace ammanfa koda munje karki nunamasa kintaba zuwa wani gurin kedai kawai aiki kikeso ayimaki kuma zai iyah Aisha✍🏼 [3/29, 10:13 AM] YAYA HAYAT: ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠ Chapter 013 By Gentle Lady💃🏽 Lubabatu tace Indai dan wannan aibanda matsala indai kinsan aikinai zaiyi shikenan nayarda komai zakice"" khairat tace yauwa tawan kokefa Amman kinazama ace kishiyarki Yaya uku wannan zurare kamar akuya""! Lubabatu tace kemadai kyafada wannan kafin aje ko ina zatacika gidan tana haifo uku uku kumafa karkiso kiganta kamar lagwanie wlh suka kwashe da dariya tace shikuma mijinki kome yaganie atattare da itah inba jaraba tada namijiba"" Lubabatu tace aidama itane"" bari nakawo maki abinci" khairat tace ah ah kibarshi yanzun zandaga sauri nakeyi tayi maganar tana mikewa kedai sainaganki ina zuba ido Lubabatu tace insha Allah zakiganni aini dama zanice ta tararda mujemu wlh yandakikasan akan kaya nake nakijinin nabuda idona naga wannan yarinyar sainaji kamarma inshakureta kowa yahuta"" 😕 Khairat tace basaikin wahalda kankiba Abu da komai yacigaba kedai saikinzo harbakin kofa tarakata sukai bankwana azuwan saitazo sannan tadawo dakinta farinciki fal ranta saiga lubcy harda barcin rana Wanda rabonda tayi irinshi tunranarda khadija tadawo gidan"" Khadija sunacen sunacin buki Batasan anacen ana shirya yanda za a gama da itaba"" gaskiya taron sunan yakayatar da mutane anyi abubuwan rabo tundaga bokiti kwanduna darduma turame agogo shaddodi jikkuna "" dadai sauran kayan rabo"" anci ansha kowa yazo bikin yakwashi gara bakamar yan group din Haneefa dannaga dayawa cikinsu amarorine"" an iyah zuwa biki kodakuwa ba a gayyacesuba😝😝 Labila kam karshe gidan hajiya takoma wajen mama kubrah dantagaji dayawan kallonta da muktar yakeyi itah tanaganin kamar kallon rainin wayo yakemata shikuma yanaganin kamar tsabar wulakancine yasaka takewani dauke kai duk sa inda taganshi Tarodai yayi alhamdulillah kowa yawatsa anbar maijego da ya"" ranta saimuyi mata addua Allah yaraya matasu" Muktar kwanabiyu dasuna yakoma"" khadija sosai tana tausayin mijinta dantasan yanayinsa kwanansu ashirin tacewa innah zatakoma duk da nauyinda takeji Amman inna batakawo komai arantaba La akarida yawan zuwanda Usman yakeyi saitaga kamar danshine khadija ta tausaya mashi"" innah tace tadankara hakuri agama shiryamata kaya nanda kwana biyar Tundaga ranar akasoma shiryata anasaurah kwana bakwai suyi arba in su gwaggo hassana suka miyarda itah" ranar Usman kamar yahadeta Dan murna Khadija tamatsawa labila takoma makaranta hakanan zaman bazaiyimata ba tashafe shekara gida tace itah karatu indai batareda khadijaba tayafe Khadija tace tosaidai idan aure zakiyi"" kuma tace bayanzuba saida sukayi fada khadija tayi fushi sannan labila tayarda Amman akaduna zatacigaba da karatun tarika kwana agida Khadija tace batayardaba "" labila tace to Zaria fa??? Ko kano"" khadija tace zabidaya saitayanke shawarar zuwa A b u Zaria Cikin sati daya akagama komai tasoma zuwa lubabatu kamar hakan takejirah tatambayi Usman zataje gidan sajida kawai tawuce katsina batawani sha wahalaba ta gane gidan khairat din dayake ba boyayye bane mijinta kumagidan akan hanya yake Da sallama tashiga gidan babban gidane tangarere kamar wani Karamin kauye Khairat tana falonta ta amsa sallamar mai aikinta tanayimata tausa tace tatashi tacewa mai sallamar tashigo Tace to tareda mikewa tafita tagaida lubabatu sannan tanunamata inda uwardakin nata take Takaràsa tanamai sakeyin sallamar"" khairat ta amsa fuskarta tanakallon maishigowa Tana ganinta tawashe baki yarhalak kenan yanzun nagama zancenki axuci nace shirudai kodai kinsauya shawara"" Lubabatu tanazama akan kujerah tacire mayafinta tace shawaradai aisaidai idan harmutuwa nayi Amman daraina dalafiyata aibanida wata Mafita wacce tawuce wannan"" Khairat tace babu kam bari nasa akawo maki ruwa kisha idan kinhuta saimuje lubabatu tagwalo ido tace wanne irin Hutu aisauri zamuyi inkoma nafadamaki banaso idon kowa yasauka akaina afara zargina Khairat tace totashi muje damadai nidin ashirye nake muje yanzun ma baza asamu jirah sosai wajensaba dakinta tashiga tadauko mayafi sukafito Takwalawa mai aikinta kirah talatu""" dasauri tarugo tafadi gabanta tanahaki tace ganie rankiyadade"" tayatsina fuska zandanfita bajimawa zanyiba kafin nadawo kitabbatar kingama hada abincin idan alhaji yadawo kikaimasa Nashi kuma kicemasa banisa nayiba dankaryafita harsaina dawo Sauran kuma naje nadawo natarar kinbarshi da yunwa taran kwasheta aka tashi kibanie wuri tadafe kanta tamike dasauri tabar wajen khairat tatofarda yawu tareda Jan tsaki tace mujeko hajiya Lubabatu tabita suka wuce tunkafin tashiga mota maigadi ya hangame masu kofa danyasan halinta idan ranta yabaci ba Karamin aikinta bane ta gaggaurah masa mari babu ruwanta da tsufansa"" Motarta suka shiga taja atsiyace tawuce yagada mata hannu Allah yakiyayeki hajiya guntun tsaki taja tabadeshi da kurah su lubabatu kam tazama Yar kallo gaskiya wannan yaburgeta sosai itama yakamata tasoma shinfida milkinta agidanta kowa yadinga jin tsoronta Duk da mijinta yafi mijin khairat kudi nesa bakusaba Amman ita ko maigadon gidan baya tsoronta tunda tunfarko batanuna masu hakanba Amman zatasauya taku kodan surikajin tsoronta har uban gayyar Ahakan zatasamu ta tatattare kadarorin Usman tasoma kasuwanci harsuka kai dajin bokan lubabatu batasaniba saida khairat tace kifito munkawo sannan tahankalto tafito sukasake nausawa cikin jeji Dayake lubabatu tasaba ganin makamancin irin wannan dajin koma Wanda yafishi abun tsoro da abun al ajabi Sam bataji tsoron dajinba Sai hawan duwatsu sukeyi wani gurin dajan duwawu suke wuceshi danbahali kataka dakafa"" bakin wata katukar kuka suka nufa khairat tacewa lubabatu sucire takalmansu Taresuka cire sukasoma tafiya da baya baya harsukai kai wajen bokan ya umurcesu dasu zaune sukazauna shikam wannan yasha banban da *hatsabibin boka* Bayada wani jiki sosai saitarin suma akansa kamar rumbum kara"" hakoranshi jawur duk sundafe saboda cingoro dakuma kazanta kayan jikinsa duk sunyage saikace matsiyaci duk ina kudinda yakesamu Ace war lubabatu Dan *hatsabibin boka* baida wannan kazantar"" fadarsa kawai abun kalloce Amman wannan cikin kogon kuka saidan wani daki dayayi agefe nakasa" karami kamar bandakie Lubabatu tayinisa wajen karewa wajen kallo muryansa maikamada kukan jaki taji yace meke tafedaku??? Khairat tace tsafi yakara maka lafiya kajima kayi karko Kawata nakawo akan batun kishiyarta kamar yanda nafadamaka . Yagyada kai sannan yadauko wata katuwar kwarya akwai ruwa acikinta kamar ruwan jinie yakalli lubabatu yace saka hannunki nahagu Jiki narawa tatsoma hannunta yayi wadansu surutai da tsifface tsiffacensa daga bisanie yace tacire hannunta" Tacire yace yasunan kishiyar takie??? Tace khadija mijinkufa??? Tace Usman"" Yayi Zane saman ruwan sannan yakalleta yace yakikeso ayimata, ?? Lubabatu tagyara zama tace ran boka yadade nidai inson samunane akasheta daga itah har yaranta"" Yajinjina Kai sannan yasakeyin rubutu yashafe yasake yinwani zuwa mintuna kadan yarufe idonsa yasomayin wadansu surutai yana girgiza kai tsayin mintuna biyar sannan yadago duk yayi jibi kamar Wanda yayi wasan tsere yakalli lubabatu wacce tamatsu taji mezaice idanuwanta zuru zuru kamar wadda taiwa sarki karya Kuyi hakuri dawannan wlh banda chaji yau. idankuma NEPA tadawo kafin dare zakujinie Aisha✍🏼 [3/29, 8:28 PM] YAYA HAYAT: ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠ Chapter 014 By Gentle Lady💃🏽 Yace gaskiya aikinki yanada wahala" kuma akwai hadari sosai acikinsa" lubabatu takallikhairat race bana fadamakiba "" ai wannan yarinyar tunda ta Gagari hats"" Khairat tayi maza ta zungureta tace ranboka yadade asake dubawadai ataimaka mata kawatace"" yajinjina kansa sannan yasake yan tsiffacensa yace wanan yarinyar dakuke ganie gabadaya jikinta haskene aiki da irinsu yanada hawalar gaske Dan aljanu ma Kansu tsoron rabarsu sukeyi intakaima aljanie yamatsa bashakka zairasa rayuwarsa Wannan yanuna koda tanajinin al ada bataxama sakaka kullum cikin Neman tsari take danhaka kasheta gabagade bazai taba yiyuwaba saidai akwai wata mafita daya idan kinji zakibita meyiyuwa zata bulledake Tunkafin lubabatu taji menene mafitar tace nidai komenene ayi indai zatamutu banda Matsala"" bokan yajinjina kai yace hanyar itace zanbaki wani garin maganie nagubar aljanu"" kibarbada mata kofar dakinta Saiki koma gefe kikirata kilabe dazaran tafito tataka maganin koda kadanne tozata fadi awajen tayita mulmula"" shikenan zata tashi kamar bakomai saidaga baya zatarika jin kaikayi ajikinta Duk inda tasosa kurji zaifito dazaran kurjin yafashe ruwan suka tabi jikinta wasu kurajen zasu sake fitowa kuma idan tabarsu zasurika girma harsu zamemata gyambo Tarika wari yanda kowama baya iyah zuwa wajenta dagakarshe ciwon zai kasheta kinga kinhuta Amman ki kula karkibari wani yatsilga maganin indai ba ita ba zaisake magana tace kwantarda hankalinka aibana kuskureba! Yace kinason mai makari kokuma Wanda baida makari??? Tayi saurin Tatar nunfashinsa tace wanne irin makari ai makarinsa mutuwa boka aini banason tawarke yace shikenan an gama ammanfa aikin nan yanada wahala sosai"" danhaka zakibada kudi tace banda damuwa dasu nidai bukatata tabiya yace an gama yadaga hannunsa sama yaruntse idonsa yasoma wadansu surutai marasa dadinjin bamakagane meyake fada"" saiga wani kullin maganie yafado ahannunsa cikin wata Leda yake sannan angefashi cikin battar kwarfe yamika mata dahannun hagu yace kirikeshi karkisake yataba hanun dama harsaikin kai gida kina iyah aikidashi yau kogobe Amman dazaran yawuce kwana biyu yatashi aiki kikula karkibari wani yaketara inba itaba danduk Wanda yatsilga shine zaiyi wannan jinyar kodakuwa kece Lubabatu tace Allah mayakiyaye intsilga tsawa yadakamata yace ba a kiran sunan Allah anan " khairat tace tuba muke boka batasaniba bakuwar zuwace Atsawace yace ta aje abunda tazodashi subacemasa daganie jiki narawa lubabatu tazuge Jakarta tazubemasa kudin duka suka mike yace kutafi dabaya kuna tsalle jiki narawa suka juya suna tsalle gashi lubabatu katuwa da itah nan take tasoma hakie saida suka daina ganin kogon kukar sannan sukajuya Wannan karon wajen haye duwatsu lubabatu harda kuka danta wahala wajen tallen nan"" suna kaiwa gunda khairat ta aje motarta suka shiga suka kama hanya"" Sunata nosawa cikin jeje Ashe dajin yanada nisa bata lurah da hakanba saiyanzu kamar dagasama sukaga tarin ayarin yanfashi Hantar cikin lubabatu takada tace yanfashi darana tsaka??? Kafin tayi aune taji sunharba bindiga take khairat tataka burki babbansune yadaka masu tsawa yace kufito jiki narawa suka fito Akace sukwanta suka kwanta duwawun lubabatu sai mazari sukeyi tunda take bata taba ganin bala I irin wannan ba babbansu yabada umurni aduba motarsu komai akaganie adauko Dayake basuzo dakudiba kudin khairat daine dasukasamu dubu hamsin"" dawayoyinsu daya dagacikin yanfashin naga yaje wajen ogan yayimasa rada akunne Yayi dariya yace kahuta usher"" aisunacikin ganiyarmu" kahole kawai"" Wanda naji ankira da usher yakalli lubabatu yace tatashi Sam Batasan niyarsaba tamike yatasa keyarta cikin wata bishiya maiduhuwa yace tacire kayanta Idanuwa kulu kulu😳 tace ban....ban.. gane incire kayanaba mezakamun"" cikin muryarsa tamashaya yace ke hajiya zakitubene kosainayi maki takarfi idan bakiganeba kibari nizan nunamaki yasoma zuge wandonsa Saiyanzu lubabatu tagano abunda yakenufi tafashe dakuka😭 taduka harkasa tace karufamun asiri wlh bantabayin iskanciba banama ra ayin wannan arayuwata konawane nizan baka Amman kabarni natafi Yace ke hajiya bamagiya nakirah kiyimunbà kiyimaza sauri nakeyi Dan amatse nake" lubabatu tasake rudewa taciro yan kunnenta nazinari dasarka duka tabashi akan yakyaleta ganin tana nema tabata masa lokaci yakirah wasu acikin tawagarsu suka riketa yabiya bukatarsa takarfi sumakuwa sukaçe saisun Dana kato shida yataka lubabatu wanima sau biyu yayi dayake su goma sha biyune saisuma shidan sukahole da khairat Anan suka barsu sunata kuka bakamar lubabatu tayi Allah wadarai dazuwanta wannan dajin abunda take hanawa mijinta yana roko yana karawa Yaugashi wadansu kartin banza batasan kosuwayeba kazamai sunsameta sunyita jijjiga kamar injin Wankie kuma harda maroranda tasha duk na iska gashikuma suntafi da sarkarta Duk wannan wuyarda lubabatu tasha batayarda tasaki kullin maganin nan dayake jikin battaba"" khairat tafita karfin hali tamike tamiyarda kayanta tarikata tatashi tamiyarda zaninta sukawuce wajen motarsu lubabatu babbare take tafiya saboda abun bana arziki bane hardajini fita yakeyi kamar anbare budurwa Sukashiga mota khairat taja lubabatu kam sairusar kuka take harsuka kai gidan"" bayan anbudemasu kofa sukashiga tayi fkng tajuyo tana kallon lubabatu tace haba Kawata saikacee bamaceba baidace Dan wannan yadamekiba Kituna abunda kikaje karba kuma kinyi nasara nanda kwana uku zakidaina jin wannan radadin Amman kishiyafa harkimutu bazakidaina jin zugintaba Lubabatu takalleta da idanuwanta dasuka rine kamar gauta tace khairat kinsanni batun yauba nibana harka damaza harnayi aure garake kinsaba dakwana danamiji biyar komafiye Wlh ni dayanma bana iyawa Usman hakuri kawai yakeyi danie dalilinda yasaka yakara aure kenan"" yanzun takaicina daya Kawata wadannan kattin bansan cutarda suke dauke da itaba kar ace sunada kanjamau sulikamun mugun Abu ina zaman zamana Khairat tace manta basatare dakomai nikaina nayi barikin harnayi aure bankwashi cutar komaiba saike da akayi saudaya dake kinga kishare hawayenki mushiga gida kiyi wanka kigasa jikinki tayanda zakiji dadinshi saikiwuce gida Lubabatu tace to sukashiga gidan mijin khairat yana nan zaman jiranta tace yabasu wuri tana tareda bakuwa yace to sannan yagaida bakuwar yafita tasa mai aikin tahadama lubabatu ruwan zafi tagasa jikinta taci abinci tadan huta sannan sukai sallama da khairat tashiga motarta tayi kaduna Ana kiran magrib takai gida tanata addua Allah yasabakowa falon cikin sa akuwa batasamu kowaba tahau Na uwarda zata sadata bangarenta tanashiga tasaukarda ajiyar xuciya kayanta ta aje tarage kayan jikinta takwanta saibarcin gajiya Usman baidawo gidanba sai karfe Tara falo yasamu labila da khadija suna firah su anwar sundade dayin barci nan khadija tabar labila taje dakinsa tahadamasa ruwan wanka saida yakimtsa suka sauko dancin abinci yace ina maman Abdul bangantaba?? Khadija takalli labila suka kalli juna yace menene kuke kallon kallo?? Khadija tace tunda tatafi unguwa batadawoba ai"" yace injiwa bayan ga motarta nan naganie awaje yayi maganar yana wucewa zuwa bangarenta" Dasallamar sa yashiga yasameta kwance saman gadon yazauna yasafo fuskarta ahankali tabude idonta murmushi yasakar mata Yace kekadai mukejirah muci abinci gashi harkin kwanta" Ta muskuta tace bazan iyan cin komaiba agajiye nake wlh jikina duk ciwo yakeyi"" Yace subhanallah me take damunki?? Tayakuna fuska wlh aiki Nataya sajida tahadawa kanwarta cincin shinefa jikina yake ciwo yace ayya sannu bari nadanna maki Yatankwashe hannun rigarsa yahaye kan gadon yasoma yimata tausa"" sosai takejin dadin tausar su khadija sunacen sunazaman jiransu ba Usman ba lubabatu kowannensu yanayi yana kallon ago go kadan kadan labila ta[truncated by WhatsApp] [3/29, 8:28 PM] YAYA HAYAT: ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠ Chapter 015 By Gentle Lady💃🏽 Bayan kamar mintuna goma labila takalli khadija tace kinga sahiba babu amfanie wannan jiran muci namu muje mukwanta Murmushi kawai khadija tayi dankuwa ranta yasosu dawan nan abun Amman kuma batason nunawa labila dankartaji wani iri" Usman yasan girkinta ne Amman yaje dakin lubabatu yayi zamansa saikace ranar girkinta Saida labila tasakeyin magana tukun Khadija tazuba masu tasan bawani cizatayi dayawaba Amman hakan tayita wasa da chokali har labila talura takirah sunanta Sahiba khadija takalleta daguntun murmushinta tace yadai sahiba?? Labila tanisa tana aje tsokali tace kiyi hakuri" khadija tasake murmusawa tace da...akayi mekuma?? Labila tace nasan kinsani Amman kiyi hakuri nikaina abun nan baiyimun dadiba Dan gaskiya dad bai kyautaba duk danasan balaifinsa bane akwai sahannun mom Khadija tayi Sako tana saurarenta kenan tana nufin maganie mom tayiwa Usman??? Komadai menene zataganie daga baya idan taga yacigaba dahakan tozargin gaskiyane Tanisa tana kallon labila tace bandamuba sahiba bakisan menene yatsaidashi ba kirika yiwa Mutane kyakkyawar fahimta mana Tasoma cin abincinta ganin hakan yasaka labilama tasoma cin nata harsuka gama usman bai saukoba sukayiwa juna saida safe kowa yawuce inda zaikwanta Dayake labila bangaren lubabatu take kwana saida Usman yaji motsinta"" sannan yataso Dan lubabatu tadade dayin barciii Kallo daya yayiwa labila yasan akwai Matsala Dan dauke kanta tayi tashige daki" yayi shiru waima meyasa yadade harhaka ??? Sam yamanta suna jiransa jiki sanyaye yasauka kasan baisamu khadija ba saiyawuce bangarenta Itakam harta kwanta rigar jikinsa yacire yahau saman gadon yakwanta gabanta yanda zai iyah ganin fuskarta Yajawota jikinsa Sam batacemasa komaiba kuma batayi kokarin jaye jikintaba"" andauki tsayin mintuna ashirin yakasa barci saijuyi yakeyi yasake kallonta idanuwanta arufe suke bazai iyah tantancewaba barci takeyi kokuwa idonta biyu Sunanta yakirah Deejarh Na" bata amsaba saida yasake kiranta sannan ta amsa batareda tabude idonba Yanisa kikalleni Dan Allah Deejarh na"" yamarairaice murya Dan murmushi tayi sannan tabude idonta ahankali takafa masa ido Tuni yasanne kansa kasa Dan abunda yaganie acikin idon khadija "" baice komaiba tagajie dajin shirun tace kaci abincinka kakwanta nima barci nakeji tanakaiwa nan tasake gyara kwancinta Usman yarasa yazaiyi yace khadija maganafa zamuyi Tace dad abar maganar nan saigobe barci nakeji yanzun" kafadarta yadafa yace tokiyi hakuri Dan Allah Tasaki lallausan murmushi tace laifin me kayimun?? Ina anabada hakurine gawanda akayiwa laifi nibakamun komaiba karma kasadamuwa aranka Yasake sukurkucewa yace Nina San nayi laifin ai tunda nanemi ayafemun wlh bazan iyah yin barciba inhar bakince kinyafemunba Danaje kiranta nasamune batada lafiya aikisukai gidan kawarta jikinta yanamata ciwo shine nataimaka nadan daddannamata"" Khadija tace hakan yanada kyau Allah yahutarda gajiya ""😑 sosai Usman yasan khadija da ma ana biyu take yin magana yace bawan nan ba nidai kice kinyafemun"" Takalleshi tace tonayafe maka shikennan ko saida safe"" yasake bata fuska"" tace menene kuma?? Yace kincemun saida safe yanzun haka zakibarni Tome zanyimaka nibarci nakeji" kenan baki hakuraba??? Wayafadamaka??? Aidakin hakurah dabazaki hanani abunda kikasan nafisonsa fiye dakomaiba Hannu tasagalo masa awuya tace kafin nan yakamata taci abinci dannasan kanajin yunwa"" kaiyagirgiza yace bazan iyah cin komaiba yanzun kina wannan yanayin lumshe idonta tayi sannan tabude tana kallonsa sannan tamike tadaurah zanie tafita shima yamike yabiya abaya harkasa tazubamasa abincin tajuyo sukadawo tare Dakanta tarika bashi abaki haryakoshi tamiyarda kayan yayi brush sannan suka kwanta *********************** Washe gari tunsafe suka gama hada kayan break labila kam dataga khadija tasakewa Usman haushi tabata nikam nace baki iyah shiga tsakanin mata damiji Taresuka zauna cin abincin Usman ne yafara tashi danyana sauri zaije company yau akwai bakinda suke saran zuwansu akan wani hadin guiwa"" khadija tarakashi harbakin mota tayimasa adawo lafiya tadawo sukacigaba dakarya warsu labila ma takoshi tadauki littafanta tawuce akabar khadija da lubabatu Khadija takwashe kayanda suka bata tamiyar kitchen tadawo tahaye sama abunta lubabatu dadi yakumeta tatashi tahau saman tadauko battar takarasa bangaren khadija" da sanda tabude battar tabarbade maganin duka sannan takoma dabaya dakwallawa khadija Kira Tana kwance kusa dasu anwar taji kamar mom takirata tamike zatafito kawai sapna tabare baki tasoma kuka"" nafitar hankali kamar wacce akaciza Dasauri khadija tadawo tadauketa saitayi shiru "" lubabatu tasake kiranta dasauri tamike tareda sapna tawuce Anwar da husna suka kata kusan atare harda sapna din dolenta khadija takoma tamarasa yazata daukesu duka Lubabatu dataji shiru saita dauka khadija batajibane tadawo kofar dakin tasake kwalamata kirah kamar wani yaturata saikawai tazame tafadi dabas kafafuwanta suka tabi maganin saiga lubabatu tana mulmula akan maganie Data hankalto damenene yasameta tafasa ihu nashiga uku na lalace🙆🏿 " wannan Kalmar da khadija taji yasaka tayi saurin ajesu anwar tafito dasauri wannan karon su anwar wasasuke dayatsun hannunsu basuyi kukaba Ganin halinda mom takeciki yasa hankalin khadija yatashi tace hasbinallahu wa ni imal wakil mom meyasameki??? Sai lokacin akadaina jujuya lubabatu Tayi saurin mikewa idanuwañtà zuru zuru tace bakomai dama zance idan kinyi ajiyar maganin ciwon jiki kibanie sainazame anan Khadija tace Allah sarki wlh fitsari anwar yasaki dazu awurin shine nagoge daruwa Ashe akwai sauransu sannu gashikuma banida maganin Amman barinakirah baban sapna saiyaturo yaronsa yakawomaki Lubabatu tace ah ah kinjifa yace sunada baki baridai nahakurah zuwa anjima khadija tace shikennan lubabatu tawuce tana dingishi khadija tabita dakallo cikin tausayawa tajuya dakinta Lubabatu dasauri ta isah bangarenta tayarda battar tacire kayanta takulle daleda tafada toilet takwarawa jikinta ruwa Tasa so so tayita darzar jikinta saida tayi sabi goma shabiyàr sanan tafito daure da towel tana tsane jikinta Aranta tace shegen yaro yatsula fitsari gashi yabatamun tsari dole sainakarbo wani kuma taja tsaki badaihakan nasoba Tasoma duba jikinta ainasan babu abunda zaisameni tunda nawanke tàsau kàrdà ajiyar zuciya saiyanzu tajisanyi aranta ganin tawanke maganin kuma bataji wani sauyinba""" Ajikinta kwanciya tayi tanata yan tunani harbarci yadauketa" bata farkaba saikarfe biyu qalau tatashi tayi" wanka tasauka taci abinci alokacin labila tadawo tazauna cikin falon suna kallo har Dare bataga komai ba saikawai tasaki ranta dama tasan dakyarne idan aikin bokan nan zaiyi kawaidai yacimata kudine abanza Taresukayi lunch dadare bayan suntaba yarfira kowa Yakoma dakinsa yakwanta"" Suna kwance Usman yana wasa da gashin kanta yakirah sunanta" ta amsa yace albishirinki"" tace goro fari Kal yace nashiryamaki tafiyarki Niger gobe kuma nasanarda"wani abokin kasuwancina dazaran jirginku yasauka zaizo yadaukeki duk inda zakuje taredashi zakuje banason kisha wahala kafin kugane inda take Khadija tace kamanta gidan sarautane aibazai boyuba"" yace hakane Amman aikince batagidan tunda bayan barinta nandin bagida takomaba Khadija tace hakane kam Amman najidadi sosai mijina""zanyi kewarka yace bakiji mamaki danasauya ra ayiba nantake??? Tace najimana Amman bankawo komai araiba Yamurmusa tafiya takamani gobe kuma sati daya zanyi america zanje akan harkar da zamuyi dama banafadamaki munyi bakiba??? Khadija tace ah yace akwai tattaunawarda zamuyi sunason kafa company a kano shine zamuyi hadin guiwa komadai yamukayi idan nadawo zakiji tace to Allah yabada sa a yace Ameen Tonaso najedake saidaikuma wajen maza zasuyi yawa danba hotel za azaunaba shiyasa kawai nacebari nashirya maki kiwuce nima saina wuce"" Ammani saida yamma"" jirginmu zaitashi gobe warhaka kina niger ko??? Khadija tarungume usman cikin jindadi damurna tasomayimasa kiss tatonowa kanta dankuwa shimai gabadaya yayi""" ********************************lubabatu ta sakeyin wankatabi lafiyar gado Misalin karfe dayan dare lubabatu tasomajin kaikayi Cikin barcinta tasoma sosawa cen kuma tasakejin wani gurin yasoma kaikayi cikin barcinta tahau soshe soshe cen taji kurji yafito"" aizunbur tamike zaune tasoma duban jikinta duk inda taji kaikayin tasosa ga kurjinan yafito hankalinta yayi mugun tashi tanajin wanigun yana kaikayi Amman taki sosawa kaikayin yayi yawa batasan sanda tahau sosawaba Kuma idan tana susarsu wani dadi takeji gabadaya jikinta Yakama yam yam yam idan tasosa nan sainan yakama tazama kamar mahaukaciya dagudu tafada toilet ""'tahada ruwan zafie tawatsawa jikinta saitaji sauki sauki tagoge jikin tadawo takwanta Kwanciyarta keda wuya gabadaya jikinta Yakama kaikayi"" harcikin kai""" Lubabatu barci ya gagareta takoma gefe tanata kartar jiki kamar maiciwon kazwa"" Aisha✍🏼 [3/29, 8:28 PM] YAYA HAYAT: ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠ Chapter 016 By Gentle Lady💃🏽 Idanuwanta biyu har akayi kiran asuba tanaji Usman yana buga mata kofa tatashi tayi sallah "" tacemasa to mikewa tayi takunna wutar dakin ganin kurajen minini ajikinta tasoma binsu dakallo "" gabanta yana faduwa dole takoma wajen bokan nan tunkafin abun nan yayi nisa yakareshi "" Nikam nace kinmanta kincemasa Wanda bayida makari sai mutuwa?? Dama ance idan zakagina ramin mugunta kaginashi gajere dankoda kai kafada zaiyimaka saukin fita Wanka tasakeyi saboda kaikayin tasaka kaya masudan tsayi duka sunrufemata jiki tayanda babu Wanda zaiganie Karamin hijab tasaka saboda wadanda suke awuyanta"" tana zaune sai sake sake takeyi har haske yafito Usman ne yashigo dakin da sallama ta amsa tana dago kanta Kusa da itah yazauna race masà inakwana" yace lafiya qalau kintashi lafiya?? Aranta tace bakalauba shegiyar matarka tanason ganin bayana"" 🙄 Afili kuma tace qalau saidai kewarka"" murmushi yasaki cikin jindadi yace kitaso mukarya Dan khadija Niger zataje wajen dangin mahaifiyarta" Tace waidama ita Yar Niger ce??? Yace ah kishiryamun kayana kafin nakaita airport Dan nima tafiyace takamanie mutanenda nafadamaki sunzo company jiya tosune sukahada mana zama a America akalla zanyi sati acen Lubabatu tace shikenan suka tashi suka sauka kasa sunsamu su khadija harsun soma karyawa tazuba masu sannan tacigaba daci Duk da zumudi baibarta taci dayawaba"" tana gamawa labila tatayata suka dauko kayan labila taso tabita suje tare Amman gobe zasufara jarabawa shiyasa kawai bazata bitaba harbakin mota lubabatu tarakasu tanayiwa su anwar adawo lafiya Abunda zaibaku mamaki su anwar basayarda lubabatu tadaukesu dazaran tadaukesu saisukama ihu dole sai an karbesu hakan yasakama tadaina daukarsu Khadija tace shegiyar kiuya kamar wadanda akexizo lubabatu saidai tace hmm kawai saida motarsu tabar gidan sannan takoma cikin gida . Sunje adaidai kuwa suna isah akagama komai khadija takude jirgi su labila sunatsaye hargirjinsu yadaga nikam nace khadija dakarfin hali yara uku kuma babu mairike mata kodaya Amman tunda tasaka ranta datafiyar aisaitayi tanason ganin kaleed ne sosai "" Karfe biyu jirginsu yasauka" Niger tana saukowa tasoma kalle kalle inama zataga mutumen jitayi anyimata sallama"" ta amsa dafara a yace madam nine Wanda akace zankaiki gidan Tace okay anwar dayake hannunta nadama yakarba"" tanagoye da sapna husna kuma tana rike gahannunta nahagu motarsa yabude tashiga yasaka Kayanta bayan motar tareyake dawani da alamu driver sane sukashiga motar yatayar Sukahau hanya"" sunatafiya khadija kam sai kalle kalle takeyi " harsuka kaigidan sarautar mutumen yace wajenwa kikazo??? Tace sunanta Hauwa u yace shikenan fita yayi yayiwa maidagin bayani akasheka akasanarda sarki yanada baki daga Nigeria sunzo wajen hajiya babbane"" Yace ayisauri ashigo dasu nantake fadawa sukayimasu iso sarkin Wanda yake kan kagarar dazaran kadubeshi kaga khadija saikace shine yahaifeta dankamar tasuma tabaci yana ganinta yamike yasaki fara a Yanayimata lale marhabin"" anwar yakarba yana kallo yacewa fadawa yau manyan bakine dasu danhaka zaigana da bakinsa kaitsaye cikin gidan yawuce dasu wajen matansa sukuma wadanda suka rakota yace akaisu falon baki akarramasu Sosai khadija tashiga mamaki ya akai yasanda zuwanta babban gidan sarautar cike yake damanyan ginuka ko ina Kaduba bayine gasunan sunata aiyuka Kaitsaye turakar Fulani yanufa itace uwargida "" itama tanaganinsu tatashi daga kishin gidenda take tace wanakegani kamar khadija?? Maimartaba yakalleta da murmushi akan fuskarsa yace itace ina hajiya?? Tace yanzun nan takoma bangarenta saimuje cen kawai tamike ta umurci sauran bayin dasu sanarda Amarya gabadaya suka rankaya dakin hajiya Duka yaran khadijar andaukesu anwar yana hannun mai martaba husna tana hannun Fulani sapna Amarya takarbeta Ita haryanzu mamakine kwance akan fuskarta sunashiga tayi arba da dattijuwar data taimaka mata lokacinda take nakudarsu Husaini Itama tana ganinta tasaki fara a"" dasauri khadija taruga tarungumeta saikuma tafashe dakuka"" tashafa bayanta tace menene nakuka aikindawo cikin yan uwanki Cikin kuka tace dama Ashe kece kikahaifi mamana meyasa bakifadamun hakanba lokacinda muke cikin dajin zaune??? Tadago da itah tana murmushi tace khadija kenan ba maimunatu tasanardakeba abunda yasaka banfadamakiba nasan idan kikaji zakiji haushina saboda duk nice silar shigarku wannan damuwar Saiga hawaye sunabin fuskarta Fulani da mai martaba suka zauna tareda Amarya"" Khadija tasharemata hawaye tana girgiza kai tace kokadan bakece silar damuwar muba kowa naduniya bayawuce kaddararsa Kaddararmuce tazo dahakan"" Hauwa u tafashe dakuka tace inada laifi sosai gashi asanadin rashin bin iyayena nayisanadin da yata Tarasa ranta bazantaba gafartawa kainaba wannan bakincikin dashinake kwana naketashi Najamaki gashike bakisan dadin uwaba kowayanaso yatashi tareda mahaifiyarsa itah tarayu babuni kekuma kinrayu babu itah mezaisa bazanyi kukaba kaichoni hauwa Nina San har abada bazandaina kukan nanba"" khadija tace dangirman Allah kidaina cewa hakan babufa Wanda ya isah yakaucewa kaddararsa Kinmanta da Allah yadauke ummana yabarmun Yayana Wanda yakesona fiyedakomai yazamemun uwa uba Bantaba kukan maraiciba harnakanji araina abunda yakemun komai uwama bazata samu hakanba Yayimun abunda babu Wanda zaiyimun sannan Allah yahadanie da labila wacce takesona fiyeda kanta ""saikuma yasake hadani da Miji nagari"maisona duk wannan gatane da""Allah yayimun"aiwan nan kadai ya isah ingodemasa "" Hauwa ta share hawayenta tace hakane Amman nikam inaji ajikina bankyautaba gashi naja kinrabuda yayanki yan kananu lokacinda yadace kirungumesu sunyi nisa dake Khadija tayi dariya tace kuma Allah saiyasake bani wasu tayi maganar tana kallonsu anwar sai lokacin Hauwa tagansu daibayan daya take kallonsu baki bude tace yara uku kikasake Haifa?? Kai masha Allah "" Allah abun godiya mikomunshi Muhammad inganie tayi maganar tana kallon mai martaba yatashi yakarasa gabanta yaduka sannan yamika mata Tace barakallah kyakkyawa dashi shiru tayi tace kuganemun nikuwa kamar nasan maiwan nan fuskar??? Fulani tace nikaina hakan nakerayawa araina Maimartaba yace narigaku azuciya tunsanda sukashigo naraya hakan" Amarya tace waiku bakugane dawa yake kamaba?? Ai ina ganinsa naga kamannin sultan"" Maimaitaba yace wanne sultan din??? Tace nagidan Yaya Husaini mana"" Hauwa tace hakane Kuwa wlh sunyi kama da kaleed ikon Allah kunga yanda akeyin kama Khadija tana saurarensu saiyanzu tayi magana tace aidole suyi kama mana tunda kaninsane"babansu daya Gabadaya suka kalleta da mamaki sukace taya zasuzama uba daya kuma bayan ba ubansu dayaba??? Khadija Tanisa tace abunda yakawoni kasar nan kenan akan maganar kaleed din tanisa mahaifin kaleed shine mijinda nake aure Idanuwanta suka kawo kwalla tacigaba matar uba wacce takeneman ganin bayana itace tarabashi da mahaifiyarsa aka kasheta sannan shima tasaka akasheshi saita fashe dakuka Tundanake arayuwata bantaba ganin mace marar imaniba irin lubabatu gabadaya jikinsu yayi sanyi tasoma basu labari duk yanda aljana maimunatu tasanarda itah Aisha✍🏼 [3/30, 6:14 AM] YAYA HAYAT: ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠ Chapter 017 By Gentle Lady💃🏽 Mai martaba yajinjina kansa yace Amman kewayafada maki wannan labarin??? Ko wajensa kikaji??? Tagirgiza kai tace shiyanzu baimasan yanada yaro kaleed ba haka baisan yataba aureba kamar yanda suka mantardashi matarsa mahaifiyar kaleed Nikaina hakan taso ayimun saidai Allah baicika mata burintaba"" mainartaba yace lallai nayarda haryanzun akwai sauran jahilai aduniyar nan kodayake bazasu kareba ai yanisa Amman taya zakifahimtar da yaron nan dantunda yake baitaba sanin basune suka haifeshiba yanada shekara biyar aikomai yamanta Amman bari akirah yayan kiji yakalli fulanie yace saka akirashi yanzun harda maidakinsa tace to sannan tamike tafita Wata baiwa takirah tace tayimaza gidan sarkin fada tace anakiransa inji mai martaba"" tace angama rankiyadade dasaurinta tahanzarta domin cika umurnin uwar dakinta. Ba adauki tsayin mintuna ashirinba sukashigo tareda sallama Sundaukama ciwon Hauwa ne yatashi da akace anakiransu yanzu yanzu Ganinta zaune yasaka suka saukarda. Ajiyar zuciya"" mai martaba yanuna masu waje suka zauna " yakalleshi yace kokasan wannan??? Yayi nunida khadija Da mamaki yace wannan kamar na ima Amman tafi na ima fari kodai itace idanuwana ne suka soma ganin buji buji gabadaya sukasa dariya"" yakalli Hauwa yace inna koban fadi gaskiyaba??? Mai martaba yace kafada kam Amman kamace kawai wannan ba na ima bace sunanta Khadija Yar fateema yayarka wacce hajiya tabaro a najeria Zunbur yamike yace Allahu Akbar Allah maiyin yanda yaso ashedai darabon zanga jinin Yar uwata "" yamatsa yana kallon khadijar maimartaba yace bawan nan ba tazone akan maganar yaronka sultan Yace tofa Allah yasa lafiya "" yace qalauma kuwa kalli wannan yaron"" yayimasa nuni da anwar dayake hannun Hauwa" hassan yace tsarki yatabbata ga mahaliccin kowa dakomai ai wannan photocopy din sultan ne"" Yayi maganar yana Daukar anwar yana kallonsa"" mai martaba yace wadan nan yaran Na khadijane Mahaifin wadan nan yarankuma shine mahaifin kaleed tazone sabodashi tanaso tasanardashi ainahin tarihinsa ..gadai yartaka nan kaji daga bakinta" Hassan yakalli khadija yace ikon Allah sanardani yata menene gaskiyar lamarin"" ?? Khadija tasake sanardashi komai kamar yanda tafadamasu takai karshen maganarta dacewa shikanshi Mahaifinsu baisan meyakawoni nandinba dankoda nafadamashi ma zaice baidawani yaro kaleed Hassan yace babbar magana yata sultan baisan ainahin tarihinsaba nikaina naso sanardashi ganin yanda yakeson Zainab kamar me ammankuma yanaganin tunda iyayensu daya babu aure tsakaninsu Amman dagashi har itah suna mutuwar son junansu duk dabasufito suka fadaba itah yanzunhaka takasa tsayawa dakowane saurayi shidinma yanzun yakeson yayi aure danyakaucewa soyayyarta Naso infadamasa gaskiya mamanshi tahana waizantono masa miki tayiyuma idan yaji bamu muka haifeshiba yagudu yabarmu tunda bamusan inda zamuga iyayenshiba Amman yanzun tunda kinsan asalinsa komai yazogidan sauki zuginda zaiji kadanne" Khadija tace hakane yanxun yana ina??? Hassan yace sarkin buga boll aiyana filin wasa bakyarabashi da kwallo yaro kamar Dan danbe sukasa dariya khadija tace shikenan idan yadawo zanso ganinsa Wata baiwace tashigo taduka tace sarkin gida yace mutanenda suke tare da bakuwar hajiya sunce zasuwuce" khadija tamike Sam tamanta dasu Mai martaba yace batare kuke dasubane zasuwuce tunyanzu??? Tace ah ah batare mukeba abokin babansune dayake kasuwanci anan shine yacemasa idan nazo yadaukeni yakawo nan bari nayimasa godiya. Tayi maganar tanafira Sam tama rasa hanyarda zatabi tamiyarda itah waje saida tatambayi wata acikin bayin gidan tanuna mata""" bakin kofar fadar tasamesu dafara a takarasa wajensu tace harzaka wuce ??? Yace ah maigidanki yakirah yace meyasa kika kashe wayarki yakirah yaji kinsauka Nacemasa harkintsufa gidan sarauta murmushi tayi tace kaga kuwa wlh tunda nakasheta dazamu shiga jirgi namanta inkunna nafa gode yace bakomai Allah yahutarda gajiya tace ameen Sukai sallama takoma cikin gidan falon Hauwa u tasamu anjeramata kayan abinci da abubuwan motsa baki kayan marmari dasauransu"" sallah tafara gabatarwa tadan watsa ruwa taji sanyi jikinta sannan taci abincin saida takoshi tayi hamdala kuyangin gidan suka kwashe kayan dataci abincin Wayarta tadauko takunna takamo lambar Usman takirah tanasoma ringing yadaga cikin murmushi tace amincin Allah yatabbata agareka dan autan maxa Sosai tabashi dariya dansaida yadara yace kema aminci yatabbata agareki sarauniyar mata"" tace tofa yaukuma sarauniya nasamu yace sosai aikin koma gidan sarauta danhaka kedin sarauniyace Tace ah ah kam kamanta bakunta nazo haryanxu inanan matsayina"" yagidan??? Yanisa gida yayi fadi sosai kamar Rabin gari Tarausayarda idanuwanta tace bayan mom tana nan taya zaiyimaka fadi"?? Maganar kikeso kenan Aimuddin bakece awajeba komaima fadi yakemun Deejarh na nakanga duhu ya yawaita koda kuwa ranace Komai hasken waje banaganin komai kece pitilarda ke haskakamun gabana"" khadija tasake gyara kwanciya sosai kalaman mijinta suna isarda sakonda yakamata su Isar sunabin kowanne bango lungu dasako na zuciyarta Tasaukarda ajiyar zuciya tace Nima hakanne hubbyna"" yagyara kwancinsa yace dagaske bayan kuma kedin kinacikin danginki anyama zakituna dani??? Wainikam zan iyah sati dayan nan bangankiba?? Wlh yanxun ma dabanajin motsinki wani iri nakeji " Takwantarda murya karka damu nawan kaima ba anjima zakatafiba aizamudinga yin waya akai akai Yayi shiru tace banjikace komaiba"??? Tomezance Deejarh na gaskiya zanyi hakuri nasatin nan daya dole asaka sunana cikin jarumai Khadija tasoma dariya yace mekikewa dariya kuma??? Tace ah ah bakomai Kaine za asaka Cikin jarumai tosaika fadamun jarumtarda kayi ??? Murmushi yayi yagyara kwanciya yace jarumtar hakurin rashinki akusa danie mana kinsan bakaramin kokari zanyiba harsati daya banjini alallausar fatarkiba Haba dolema ayimun jaje bayan anbanie kyautar karramawa dajinjina Tace hakane zakasamu shakuruminka "" Amman saikaje filin daga tukun"" yayi saurin Tatar nunfashinta yace dama ainidin jarumine nasaba zuwa yakiiii kobaki saniba Dariya tayi tace habadai"" bakiyardaba kenan bari nafadamaki tace ah ah basaika fadaba nagane "" shima kanshi dariyar yakeyi Yace ina yarana banji motsinsuba??? Wlh nikaina bansan inasukeba tunsanda mukashigo aka karbesu bansake ganinsuba"" dasauri yatashi zaune yace yaran nawa toke kina ina zakibarmun yara kowa yana dauka Tace kwantar bawan Allah iyayena suka daukesu kokuma zuwa zan nakarbosu daga kawai anhutardanie Yace hakanma zakice kinsan bazaki iyah dawainiyar suba meyasa kika tsiri tafiyar"" dariya take ciki ciki tace waikai saikace gareka farau yaya bayan kanada wasu bayansu Yace nasanda haka Amman wadan nan namusammanne "" tace saboda??? Sunfito ta karkashin macenda nakeso fiye dakomai "" kuma jinin jikinta yagauraya da nasu kingane ai"" Tace hmm barci nakeji gashi sai hamma nake" yace badai yanzuba kyabari saidare"" tace hakane nikaina banda niyar yinsa yanzu sundan jima suna fira sannan sukai sallama taka she lambar ya muktar takirah Aisha✍🏼 [3/30, 6:14 AM] YAYA HAYAT: ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠ Chapter 018 By Gentle Lady💃🏽 Tana soma ringing yadauka tayi sallama ya amsa ya aiki yace alhamdulillah ina yarana tace basa kusa danie Ansama maki masu rainone??? Tace ah ah banagida yanzun haka ina dakin hajiya"! Yace kano kikaje kenan" Ah ah ba hajiya ta kano ba ina nufin kakata"" wacce tahaifi maman mu Muktar dasauri yamike yace waikina nufin kinganta???😀 Tagyada kai kamar yana ganinta yanzun hakama ina dakinta kwance gaskiya Yaya yakamata kaima kazo bagaka dangin muba kuma kowa naganie muna kama dashi Duk da banga yaran gidan ba da alamu basa nan nijinakema kamar nazauna anan🙂 Muktar baki harkunne yace Alhamdulillah koba komai munsamu dangin mahaifiyarmu Tace hakane yaushe zakazo?? Yadan shafo kansa yace inaso nadawo kano gabaya nacigaba da aiki hospital saboda wani dalili Khadija tace kai Amman danaji dadi Amman meye dalilin?? Yadanyi Jim sannan yace aure nakeso zanyi"" ! Khadija tace badai kasamu matarba ??? Ah to nasamu Amman gaskiya haryanzun bansanarda itah ba saboda batasona naso sanardake Amman nakasa Banaso nafada daga karshe tace batasona zanji natsanie kaina"" khadija tace karma kafara sanarda itah aini nayimaka mata Yayana"" tayi maganar tana murmushi"" Shiru yayi daga bisanie yace kowakika zabamun yazama dole agareni nasota"" khadija tace ainasani Yayana kasan Kuwa wacece?? Murmushi yayi yace basaikin fadaba nasan labila kike nufi Danban manta alkawarinku da itah ba nikuma itace nakeso saidai inaganin bazata soniba kinaganin duk sanda tasamemu tare dake saitafasa zama idankuma nasameta agurin Danashigo take tashi"hakan bayamun dadi" Khadija tayi murmushin jindadi tace"" karka damu indai sahibace zataso ka Muktar yace anya kinmanta shiso ba ayinsa dole"" Hakane Amman batadawani zabi tunda nima ta tursasanie na auri babanta aikuwa dole ta auri Yayana"" muktar abun na khadija dariya yabashi Yace batada laifi damacen kinasonsa"" kunya taji tace to aikaima tana sonka"" Itah tafadamaki hakan?? Aikobata fadaba indai tanasona zatasoka Dan kamanninmu iri dayane idan tana taredakai zataji kamar nice Muktar dai dariya kawai yayi yacedai Allah yasatasoni shine kawai fatana"" kasa aranka kasameta ya muktar. Yace shikenan adaitayani addua idan kinje wajensu hajiyar kice inagaidasu duka Tace zasuji sukai sallama takirah labila shukasha firah Amman batayimata maganar muktar ba hardare ba adawoda su anwar ba""" dayake yaran basuda fitina basa Neman mama "" Dadare tana falon Hauwa sai shigowa akeyi ganinta"" yara da manya sosai khadija tasake cikin yan uwanta harwajen takwas sannan akadaina taruwa sosai harda na ima taganie diyar inna Husaina "" tagakuma zainab dakannensu da yayyunsu kaleed ne kawai bataganie ba"" Tanashan tupa yashigo gidan da sallama yana sanye da kananun kaya sunbala in karbarsa tunda yashigo yakafama khadija ido kamar yasanta kodan tana yanayi da zainab dinsa Itama shitake kallo tana tasbihi ga Allah dayayi wannan halitta Kama iri daya kamar wada kani Haka zalika bazakace Usman ya isah haihuwar saba"" kujerar kusa da hajiya yazauna haryanzu baidaina kallonta ba,"" idanunsa suna sauka akan anwar dayake kwance yana wasa da kafafunsa Yazaro ido"" saikuma yasake murzasu hakan bai wadatarba yamike yadaukeshi yakuramasa ido daga Hauwa har khadija shisuke kallo"" Yajuya wajen Hauwa yace matar kinga abunda nakeganie kuwa??? Kodayake kinada matsalar ido balallai kiganiba "Ta harareshi tace ja irin yaro nadaifi matarka ganie idanuwa kamar gwazalma"" Dariya yayi yace haba kinsan kuwa wacce zan aurah aiduk kasarnan babu kamarta"" Tace wajen munintaba"" aikowa zaka aura bayana take dannice uwargida dariya yayi yace hajiya nashiga mamaki Ashe akwai Irina aduniya??? Yazauna kusa da itah yace daxun naga nshi ahannun baba Amman banlurah dashi sosaiba inasauri zanje siyowa zainab"" maganie ikon Allah yasake kallon shi yace wannan itace mamansa??? Hauwa tace itace sarkin surutu kanaganin baki kogaisheta bakayiba kakatse kaiko ina kaje saika saida halinka"" Baki yarike yace ikon Allah yaunaga inda akehana mutum yayi magana dashi dabakinshi wannan tsohuwar akwai takurah inbakiyi wasaba sainadauke kafata daga shashenki Tace dagadai nahuta kullum saika shanyemun furah"" yace najidai yaukam bazanshaba anyimun gori Amman zuwa gobe zanhuce""yayi maganar yana shafo cikinsa""" gabadaya sukasa dariya khadija kam bakibude takebinsa dakallo Idanma baiyi surutuba ai dasauransa Dan Usman ma surutune dashi harta muryansu iri dayane"" Kallon anwar kawai yakeyi shikuwa sai wangale bakiyake yana dariya kamar wasa yakemasa"" yace Kinganie ko hajiya shima yasan muna kama gashi yanamun dariya😁 Hajiya tace nidai kadameni da surutu katashi katafi gidanku"" ido yadanturo yace ko ina gidane awajena inama zantafi bakisanardani inda wannan lu"u"lu"un yafitoba Tace saiyanzu kagadamar tambaya to jikatace diyar antyn babanka wacce tarasu a Nigeria !" Kaleed yace haba no wonder naga muna matukar kama dawan nan yaron Ashe danane Khadija kam aranta tace kaninkadai"" yace hajiya kinsan me??? Tace ah ah saikafada"" Yace duk su fauziya da bilkisu da yaya ahmad kaf jikokin gidan nan basu iyah haihuwaba"" tace sabodame zakace haka Yace wannan Mamar lu u"lu"u itace kawai ta iyah haihuwa aceduk fadin masarautar nan babuwanda yayimun kara yahaifi maikama danie aini karnake kallon kowa dannima idan nai aure Yayana kamannina kawai zasuyi Hajiya tace to alhuda huda katashi dareyayi wannan firar ta asheni kullum sai anzohirah acikamaka kunne dasurutu babu Dan abun tabawa Kaleed yamike ya aje anwar yace tosaida safe bakuwa tunda korata akeyi yakalli anwar yace night diamond yawuce abunshi"" yana kwala kirah ina beranyar gidan nan take Kaitsaye bangaren Fulani yatafi yatasota yabata kaza gasassa yace takaiwa hajiya"" tace ya sultan assignment dinfa"" Yadafa kanta yace kikaiwa Aisha tayimaki sauri nake wajen abokina zanje"" tabata fuska nidai ah ah idan nacesuyimun dariya sukemun"" yace tokawo littafin idan nadawo zanyimaki sainaba Yar dasafe akawomaki tace yee nagode yayana Tasheka dakinsu tadauko littafin takawo masa sannan tasheka takaiwa hajiya Hajiya tace tatsaya takarba tace takoshi tajuya takoma"" khadija tace badai wannan yakecewa beranyaba??? Hajiya tace itace bakisanshi da shegantakaba"" abokiyar wasar sace incemaki duk bayakiran sunansu kowa dakalar sunanda yake Kira kema idan bakiyi saurin sanardashi ainahin matsayinkiba nanda kwana biyu zaiyimaki suna Shi bakinsa bayako ciwo kullum hakamuke dashi dadina dashi abudayane baruwansa dashiga sabgarda bata shafeshiba nitunda nakema bantabajin yayi koda musayar yawu dawaniba shiyasa yaran gidan nan suke sonsa Danyanda yake sakemasu fuska duka sauran yaran basa sakemasu kinsan manya akwai jangirma khadija tace aihakan yayi bari nakwanta barci nakeji gashi anwar yakibarci Tace aidole dazun barcinsa yatirga koda kawunki yakawoshi yayi barci"" kidau kazar dandan naki kichi"" tace nikam koshe nake hajiya kedai kici tunda tatoshiyar bakice🙊 Tasa dariya tace karkisa na ajeta gobe idan yazo inyaba masa itah afuska Khadija tana dariya tadauki anwar tace dadai kinci kinrage zafi danko bakiciba. Sai anmaki kishiyar tawuce tana dariya Saida tawatsa ruwa takwanta dayake takwashi gajiya babu jimawa barci yadauketa dawaya ahannunta tanason Kira taji ko Usman yakai Al amarin lubabatu kuwa daren sai ahankali domin kaikayin kamar jirayake takwanta yanda taga safiya haka taga dare "" Washe gari tunda safe kurajen sunsake girma hardawasu kananun Abu suna yawo acikin kurajen kamar tsutsotsi sai tsikaranta sukeyi"" illai kuwa tana sosawa daya yafashe saiga kananun tsutsa ruwan suna taba jikinta wani kurjin yabullo tashin hankali lubabatu Batasan sanda tafashe dakukaba kaya tasaka harda nikaf Dan kurajen sunfara fitowa agefen fuskarta tadauki key din motarta takama hanyar katsina *Ganie gawanie*ya ishi wane tsoron Allah Aisha✍🏼 ☠ *HATSABIBIN BOKA!!!*☠ Chapter 019 By Gentle Lady💃🏽 Koda ta isah katsina khairat tana lankwashe saman gado tana barci mijinta yana kitchen yana hadamata abun karyawa"" kamar anjeho lubabatu tafado gidan Ko sallama babu tasoma kwalawa khairat Kira mijin yace tana daki barci take kizauna kamin tafarka " lubabatu ko arzikin kallonsa batayiba tafada dakin khairat Tace tashi khairat kitashi"" tasoma bubbugarta mikatayi tana mutsutsuka ido ganin lubabatu yasaka tayi zunbur tace lafiya Kawata kikadako wannan sammakon😳 Lubabatu tace inafa lafiya khairat nashiga uku nikam wajen bokan nan zakirakani"" khairat tace kina nufin maganin baiyiba nikuwa nasan maganinsa yanaci Dan inada tabbacin haka Lubabatu tace Nima ainatabbata tunda nakai kaina nabaro kitashi muje Dan Allah" khairat tace haba Kawata komadai menene kikwantarda hankalinki dazaran muntafi komai yawuce kijirah mukarya nasan kekanki bakici komaiba kikafito Lubabatu tace wanne irin abinci zanci inacikin tashin hankali khairat dubafa kiga yanda nakoma"" tayi maganar tanacire likaf din tanuna mata hannunta dubi jikina kurajen harda tsutsotsi acikinsu Saiga khairat tafado tui akan gado tace munshiga uku garin Yaya hakan yasameki??? Wayayimaki wannan danyen aikin??? Lubabatu tamatso kwalla tace kamardai yanda bokan yace nayi hakan nayi saidai ansamu matsala maimakon itah tataka maganin nicenan nataka Khairat tahau sallallami tace haba Kawata meyakaiki yin wannan danyen aikin"??? Ta share hawaye tace tsautsayi mana kawaifa nakirah sunanta bata amsaba sainaje kofar dakin nasake kiranta dan ina tsammanin batajibane Ashe yaronta yayi fitsari tazuba ruwa tashafe baishafuba kinsan santsin tayil kawai sainaji yajani inataba maganin akasoma mirgina dani kamar cincin Nafasa kuwa khadijar tafito inajinta tafadi wata kalma sainaji andaina jujuyani ina zarginma anya bawajen boka takainiba??? Biri yayikam da mutum Khairat tace aini banga zamaba tashi muje tamike kobakinta bata wankeba taja mayafi suka fito Tacewa mijinta zataraka kawarta wani gurin idan yagama hadawa yaci yawuce wajen aiki yace to"" sukasa kai suka fita wannan karon motar lubabatu sukashiga'' Koda sukaje dajin sunsamu mace hudu"" gefe sukatsaya lubabatu kamar tatashi sama takeji bayan an gama dasu suka shiga tunkafin bokan yabasu damar magana lubabatu takwaye hannun rigarta tace boka kalli yanda nakoma kataimakeni kakare wannan asirin Tsuru yayi yana kallon kurajen daga bisani yace garin Yaya kika kuskure bayan kuma saida nafadamaki karki kuskura wani yataka sai itah.. Tace tsautsayine karabani dawannan masifar wlh ko barci rabonda yadaukeni tunshekaran jiya Kai yagirgiza yace yamukai dake??? Saida nacemaki ayimai makari kikace ah ah sai mutuwa Tayi saurin tarar nunfashinsa tace yanzun ahakan kakenufin zan tabbata??? 🙆🏿 Yagyada kai hakkun Dan banida maganinsa saidai zan iyah maki taimako daya"" tace namenene nidai bukatata inrabu dashi Yace bazaki rabudashiba sai dai kiji sauki wannan kece kikajawa kanki dakince ayimai makari dayanzu saina warware taimakonda zan iyah yimaki shine zanbaki maganie dai yanzun kijikashi saikiyi wanka dashi zakiji sauki Amman ciwon nan naki yadauremun kai ciwonda yakamata kiyi ba irin wannan bane Shi kurajene kawai Kuma bazasu dameki da kaikayiba tonaga wadan nan harda mugunyar tsutsa maicin jikin Dan Adam wannan tsutsarda kike ganie tsapappace sannan kullum karagirma takeyi Kuma duk bayan awadaya saita haihu ahankali zasuyita daduwa ajikinki gaskiya banine nayimaki hakanba kije kiyi bincike Wanda yayimaki wannan aikin bakaramin matsafi bane lubabatu bakiyamutu haka yabasu sukashiga motar lubabatu Sai sharar kwallah takeyi khairat ma takasa magana suna kawowa gida bata tsaya shiga gidan khairat ba tashiga motarta sukai sallama tawuce gida Tanazuwa tajika maganin tayi wanka dashi takoji sauki danharda barci yadan dauketa"" labila tana gidan Amman batasan meke faruwaba Danbata ganinta kodakuma tashiga dakin kwance takesamun ta batalura Sam dakurajenba . Kuma itama boyesu takeyi danbataso yarta taganie"" Khadija bayan takarya dasafe tayiwa yaran wanka "" tana zaune dahajiya kaleed yashigo centajiyo muryansa yana magana da yaran gidan"" Yadade sosai kafin yashigo bangaren hajiya yagaida itah tareda khadija suka amsa"" hajiya tace yau bazakaje kwallon bane naga kashigo tunda safe?? Yace ohh nikam ansamin ido kinmaidani mayen kwallo kinmanta yau ana aiki idan banje office dinba kece zakiyimun aikin Baki tatabe tace zuwa aikin naka naganin dama "" tonidai bawajenki naxoba mai kamadani nazo dauka dashi zantafi"" Yakalli Khadija yace maman lu"u "lu"u baya kuka ko??? Hajiya tace kaci gidanku anwar sunansa bazaka kirashi da sunansaba saiwani lu'u'lu'u"" ohhh!!! Aibansan sunansa hakaba suna maidadi yalakuci kumatun anwar shikuma saidariya yakeyi tun zuwansa"" Yaduka yadaukeshi su sapna suka kafamasa ido"" yace kudaina kallona bana daukar mata duk dadai kuma kuna kamadanie bansan yazanyi nadaukeku Ku ukuba Yasaba anwar ga kafadarsa yace kayiwa mom bye mumuntafii yayi maganar yana daga mashi hannunshi suka fita" Hajiya tace waike saiyaushe zakisanardashi ?? Mumushi tayi tace yau zanje gidan uncle idan yadawomun da anwar saikice inacen Nafiso ayi komai agabansu danzai iyah cewa bagaskiya bane"" hajiya tace kema kinsan saihakan tafaru ni wlh tausayi yakebanie wannan mata wannan mata ta cuceshi" " Basujima suna firaba hajiya takirah daya dagacikin masuyimata hidima tace tadauki sapna saita rakata gidan tace to Khadija tana gaba tana biyeda ita batakoso sujera da khadija harsuka kaigidan shikanshi babban gidane kuma jere suke dajuna Amman saboda tsayin gidan sarautar saikayi tafiya mainisa kamin kakai dayan Kamar iri dayane Amman wancen yafi girma dakyau"" suna shiga aka karbi husna daga hannunta kaitsaye wajen hutawar matar gidan aka kaita tanaganin khadija tasaki fara a saiyau tunjiya naketa buda idon ganinki Da murmushi " tazauna tagaida itah"" Ta amsa cikin sakin fuska "" kuyangin suka ajemata su sapna suka fita"" tace yau naganki dasu biyu ina anwar din?? Khadija tace yana hannun Yayansa tunda safe yadaukeshi Tarike baki badai dashi yaje aikinba??? Tace aikuwa dashi yatafi"" tace hakafa jiya yazo da Dare yanatamun surutu niharnafara barci yadameni wai bakuwarda akayi yar Nigeria tazo damaikama dashi sama sama nakejin"" maganarsa Khadija tayi dariya tace haka yayita zuba surutu wajen hajiya tayi shiru " dagabisani takalla tace naji gidan shiru bakowane??? Ayya basanan duka sunyi makaranta" zainab ce kawai agidan"" batajin dadi"" Khadija tace Allah sarki tana ina??? Tace Bari nasa akaiki bangarensu Wata baiwar takirah tace takaita dakinsu zainab tace to sannan tamike tana gaba khadija nabayanta harsuka kai bangarensu Dakinta tanuna mata sannan tajuya takoma khadija taturah kofar da sallama"" Zainab tana kwance idanuwanta suna akan waya takurawa pic din kaleed ido sai sharar kwalla takeyi"" Sam batajima sanda khadija tayi sallamaba Tsaye tayi tana kallon ta tasaki murmushi sannan tasake yin sallama dadan karfi Zainab tazaburah tatashi zaune tana boye wayar bayanta Ganin bakuwar gidansu yasaka tayisaurin share hawayenta tasaki fara a Anty kece Ashe ina kwana"" khadija tace lafiya qalau tana zaunawa kusa da itah tace yajikin naki??? Tace dasauki tana taba jikinta meke damunki zainab??? Shiru tayi batace komaiba "" khadija tasake tambayarta meke damunki??? Murya raba raba alamun maikuka tace zazzabi"" Khadija tace Amman kinsha maganie ko??? Tagyada kai ya sultan yasiyomun jiya nasha"" khadija tace yaukumafa??? Tayakuna fuska bankaryaba shiyasa banshaba Shine kikazauna kina kuka kuma me akaimaki??? Zainab tace la Anty bafa kuka nakeyiba abune yafadamun a ido😀 Aisha✍🏼 ☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠ Chapter 020 By Gentle Lady💃🏽 Khadija tasaki murmushi tace naji kitashi yanzun kikarya saikisha maganin kokinaso idan yadawo yasamu bakishaba yayi fushi dake Tayi saurin girgiza kanta tace ah ah banaso wlh anty"" khadija tace yauwa kokefa tashi maza kikarya Mikewa tayi Amman haryanzu batayarda ta aje wayartaba"" khadija kwanciya tayi akan gadon daidai kiran Usman yana shigowa Cikin fara a tadauka "" tareda sallama daya bangaren aka amsa"" khadija tace tunjiya naso kiranka wlh wayar tana hannuna barci yadaukeni Yayi dariya aishine dalilin dayasa bankiraba tunda naji kince barci kikeji"" tagyara kwanciyarta ya America din?? Yace ba dadi"" taturo ido saboda me kace babu dadi?? Danbakya kusa danie "" dariya khadija tayi Cikin jindadi tace bakada magana kullum sai wannan kamar gobenefa sati daya bagashi yanzun anyi kwana dayaba?? Yace saboda abun yadameni ai shiyasa banda magana sai itah" Amman naga alama kedin bakidamuba kinsan Allah sauri zanyi ingama komai nanda kwana uku zandawo kema kigaggauta kidawo Tace un um""tana daga kafada yace please Deejarh na "" kinsan halin mijin naki tausayamun zakiyi "" tace mubar zancen nan Tunda bakyaso anbarshi ina manyan gobe??? Tanisa suna wajen hajiya suna wasa nikuma inadaki kwance" toyar laushi koyarana saisunyi kewarki suma dasuke taredake Zainab tea ne ahannunta Amman khadija take kallo yanda take firarta da alamu tanacikin jindadi wani ciwo taji yanacin zuciyarta Waimeyasa haka dama akansamu Kanwa taso yayanta??? Kuma soyayya ta aure??? Kullum saitayiwa kanta irin wannan tambayar saidai batada amsa zuciyarta batayimata adalciba Batason kowane danamiji aduniya inba yayantaba Wanda suke uwa daya uba daya"" tasan haukace takeyi danhar abada bazata taba samunsaba Wasu hawaye masu zafine suka saukomata"" tayi saurin gogewa dankar khadija taganie Batasan tana kallontaba saida sukagama wayar tace yadai Zainab ko jikinne??/ Kaitagirgiza mata tacigaba da kurban tea kamar maishan madaci bayan tagama tasha maganie takwanta suna firah jefi Jefi harbarci yashureta"" tana rungume dawayarta Khadija tagyaramata kwanciya tamike takoma wajen hajiya su sapna ma sunyi barci batajima da zamaba kaleed yashigo anwar yana hannunsa yana barci Yayi sallama suka amsamasa yaduka ya ajeshi kusa da su sapna yayi hanyar bangarensu zainab"" Yasameta tana barcinta fuskarta sake murmushi yasaki yakaramata iskan ac sannan yafito"" yace mom zanwuce idan zainab tatashi kice tasha maganinta dazun danashigo nasamu tana barci yanzun ma haka banaso natasheta Tace sultan zokazauna magana zamuyi dakai"" yace to sannan yadawo yazauna "" tana kallonsa tace tambayarka zanyi Yana murmushi yace to mom tambayar saidakikasa nazauna"" tace saboda maganar tanada mahimmanci"" yace hakane saiyasake tankwashe kafarsa yana fuskantarta"" Tanisa akan maganar kanwarkace zainab"" gabansa yaji yabada rasss yakalleta jiki sanyaye yace mekuma yasameta??? Tace bakomai matsalarku dakai da itah tazo karshe"" dariya yayi har hakoransa sukabayyana yace mom bamudawata matsala dake da dad kunkasa ganewa Nidai abar maganar nan yayi maganar yana yunkurawa zaitashi khadija tace kaleed kasan wannan pic Usman takamo awayarta Tamika masa"" yakurawa pic din ido kamarshi ammankuma bashida wadan nan kayan hasalima shidin ba ma aboci saka manyan kayabane Yakoma yazauna yanakallonta yana kallon pic din yace mom kalli wannan kiga kamarni sak kodai mubiyu kika haifa??? Kai ta girgiza tace kaleed"" dasauri yadago yakalleta dantunda yake da itah bata taba kiran sunansaba"" talura da mamaki yakamashi Tace kanatsu kasaurareni yauzan sanardakai abunda bakasaniba "" zanfadamaka abunda mukadade muna boyemaka tsayon shekara ashirin da uku"" dam gabansa yayanke yafadi karfa mafarkin da yadade yanayi shine zaifaru dagaske?? Ta katsemasa tunaninsa dacewa magana tagaskiya bamune muka haifekaba?? Zunbur yamike jikinsa yasoma rawa yace wannan mafarkine bagaskiya bane meyasa nakeyawan yin irin wannan mafarkin Dan Allah mom kidaina fadarhaka Tadago takalleshi tasake kiran sunansa akaro nabiyu yanakallonta idanuwansa harsun kada sunyi jajir tace ba mafarki kakeyiba"" wannan maganar gaskiyace kazauna kaji mezanfada maka Jiki bakwari Yakoma yazauna tayidan jim sannan tace sanda mukai aure tareda mahaifinku muna son junanmu sosai duk da auren hadine munkwashe shekara uku muna tare bantabayin ko batan wataba abun yadameni sosai kullum sai inyita kuka nikadai tun inayi abayansa harnakai nakanyi agabansa ya shiga damuwa sosai watarana dadare muna kwance saimukaji ana bugamana kofa Mahaifinku yamike yafita yanacewa waye akai shiru kuma baiga kowaba ta gefen kofa yaleka"" saikawai yaga guguwa tatashi sama zuwa yan mintuna yaga tabace harzai koma wata zuciya tace yabude kofardai yaganie Yana budewa saiyaga wani yaro kwance shekarunsa bazasu haurah shida ba"" dakayansa agefensa saikuma farar takarda asaman kayan Hassan yaduba gabas dayamma baiga kowaba yakarasa yadauki takardar abunda akasa aciki wannan yaron sunansa kaleed gashinan nabaku kurikeshi yazama danku watarana gaskiya zata bayyana Yaninke takarda yaduka yadaukeshi tareda kayanshi lokacinda yafito nikuma danaga yajima sainabiyo sahunsa"" sainaganshi dayaro Cikin kaduwa nace wannan kumadaga ina? Ina kasameshi??? Baicemun komaiba yawuce daki nabishi guiwa sake"" yashinfideshi nikuma inabinsa dakallo da tambaya abakina yamikamun takardar nakaranta tazube zaune ina taslima nace koyaron wanene kuma Amman daganinsa nasan danmai kudine la akaridanayi dakayanda ke jikinsa"" washegari damuka kaiwa hajiya kai saitace murikeshi Allah ne yasharemana hawayenmu yabanie kai Tundaga lokacin mukarika kiranka sultan"" yasakaka makaranta Sam bakataba kukan gidaba tamkar kamanta kowanaka shekaranka biyu anan nasamu cikin Zainab Kayi murna sosai Wanda komu iyakar Wanda zamuyi kenan"" tunkana karami kakecewa ita zaka aurah dukda asanin kanka ba aure tsakaninku Idankuma wani yaro yace yanasonta saikamasa dukan tsiya harkagirma akan wannan soyayyar tanisa babanku yaso sanardakai gaskiya dankarya haramta maka zainab nicenace karyafada danzaitado maka damiki kaji ainahin yanda muka sameka! Kaleed Wanda hankalinshi yagama tashi yace yanzun mom dama bakune kuka haifeniba?? Tagyada masa kai yace Toni suwaye iyayena??? Tace wannan najikin pic din wayar hannunka shine mahaifinka"" kaleed yasake duban pic din damamaki "" yace wannan ne yahaifeni??? Yanisa Tayiyuma batahanyar aure suka sameniba shiyasa suka yardani"" Khadija tace karka ce hakan kaleed kaidan sunnane"" mahaifinku daya da anwar kamannin mahaifinku kukayi"" yayi saurin tarar nunfashinta yace bakida tabbacin haka yama akai kikasan shine mahaifina dankawai munakamà bashizaisa inyarda dahakanba kodama shine mahaifinnawa nibaruwana dashi natsaneshi tunkafin nasanshi Ashe harzai iyah yarda dansa bayankuma tahanyar aure suka haifeshi shinzaiyi alfahari harma ya iya kiran kansa uba Sam baidace dawan nan sunanba banasonsa natsaneshi Khadija ce tadakamasa tsawa tace yimun shiru kaleed Sam mahaifinka baichanchànci wadannan miyagun kalamanba ka adanasu saikafadawa lubabatu Itace tadace dasu"" yace waye kuma hakan??? Mahaifiyatace??? Tagirgiza kai ba itah tahaifekaba matar babankace ita ya aurah bayan rasuwar mahaifiyarka Amman duk abunda yasameka itace ummul haba isi tarabaka da mahaifiyarka Sannan taso akasheka daganan tasoma bashi labarinsa atakaice tunkafin tagama kaleed hawaye sukasoma sauka afuskarsa yasoma la antar lubabatu bayajin zaitaba yafemata idonsa idonta saiya nakkasata!!! Ashedai kaleed ma yanada zuciya"" Hmmmm anan nakawo karshen *hatsabibin boka* kashi nadaya* saikunjini akashi nabiyu *shin lubabatu zatawarke daga wannan sihirin datasa akaiwa khadija saigashi itah tafada??* *Shin kaleed zaiyarda yakoma wajen mahaifinsa???* *Wai ina labarin hatsabibin boka???* *ya makomar hatsabibin boka zata kasance???* *Ko su hassan zasuci galaba akansa sufito da aljana murjanatu idan sukaje dajin???* *ko aljana murjanatu zatayarda da hatsabibin boka???* *Labila da muktar zasuyi aure kuwa???* *Ya labarin kishiyar Fateema mahaifiyar khadija dakuma mahaifinta???* *yalabarin soyayyar kaleed da Zainab???* *ina Labarin garba dakuma matarsa huwaile wacce tayita ganawa maman kaleed azaba* *faruq kanin muktar shinkoyana raye???* *menene makomar lubabatu maikan doya???* Duka amsoshin wadan nan tambayoyin sunacikin *hatsabinin boka* kashi nabiyu kubiyoni danjin cikakkun amsoshin tambayoyin taku mai kaunarku Aisha Ibraheem Sakon gaisuwa zuwa gareku yan group din *NISHADI GROUP* *ZANGON LABARI* *MUMBARIN HAUWA JABO* *Clever's writer's* *M khady novels* *Littafan hausa* *Feedy luv novels* *Novels only* *Zuhurah novels* *Herwwerh Jeedah fans* Inakaunarku kamar yanda kuke kaunata Aisha✍🏼