*HAMSHAƘIYAR UWA🧕🏻* *NA* *HALIMA ABDULLAHI K/ MASHI* _PAID BOOK_ _Kuɗin karatu ₦600_ _Account number 0700549935 Halima Abdullahi Access Bank a turo shaidar biya ta wannan number 08140004302 ko katin Mtn_ _Phone 08140004302_ *DOKA* _Ban amince wani ya ɗora littafin nan a wani Social media ba,ko a maida mini shi Audio ba tare da iznina ba yin haka daidai yake da fuskantar fushin hukuma. A kiyaye_ *Masu son a Tallata masu hajarsu suyi magana ta wannan number 09068032427* *Page 11* Maman Nana ta gyara zama sannan ta ce, "Ni dai a tawa shawarar abin da na ke ganin za muyi shine muje mu samu Hajiya uwarmu ce mu faɗa mata cewa muna son ta yi haƙuri da waɗannan al'adun yanzu zamani ake ciki. Shamaki ya yi sauri faɗin ai kina ba Hajiya hujja da zamani kin tashi duk wani bayanin ki na baya ya ɓare. Sanna duk bayani sai kin bata hujja. Maman tace To Kinji Maman Iman. Fatima tace aini nama rasa wane tunani zanyi domin duk ta inda ka zagayo Hajiya ta riga ta bi ta wuce, sai dai mu yi ta bakin Maman Nana Muje babu hujja ɗin, mu buƙaci kawai ta bar waccan al adar harma mu bata misali da Afra tunda ta san da maganar. Duk suka yi tsit kowa na nazari, suka maida kwallon su kan A'isha Ta yi ajiyar zuciya sannan ta ce, Ni kuma nawa ganin kar muje mu tsaya mu fidda yadda za mu tare matsalar in ta faru. Misali shi Shamaki ko yaya ya samu matarsa sai ya faɗa mata cewa budurwa ce, in ma jini ta ke buƙata sai mu tanada shi mu aje. Batun girki kuwa sai mu rubuta mata a waya mu tura mata tana karantawa ta na yi da taimakon su Juma. Kunga mu fita a tunanin ya zata kalli abin kuma wane hukunci zata mana in muka tunkare ta da maganar. Kamar kowa zai amince da haka. Amma sai Shamaki yace ai bata taɓa bukatar ganin jini ba. Sannan da na mata ƙarya take take ganewa kuma ku kun sani hakan sai ya fi komai zafi a gurinta.Sai dai ɓargaren girkin in kuna ganin zata iya fahimta ita Babyn sai ayi hakan. Maman Umar ta ce Ni kuma nafi yarda da muje mu sameta mu ɗan latsa mu gani ko zata yarda. In munga alamun bazata yarda ba sai kawai mu watsar da maganar mu bi abin da addu'a. Dan abin ya zo a ƙurarren lokaci ne ai da mun saka ita yarinyar gurin koyon girki ko wata ɗaya tà yi." To haka dai shawara ta tashi ba tare da sun samu mafita ba, amma sun yanke cewa za su je gidan Hajiyar a jibi su ɗan latsa in da laushi sai su yi maganar. Maman Afra har ta fita ta dawo, tace da Maman Iman ki zo mana da kayan mu gani a gidan Hajiya. Maman Umar tace wane kayan me? Na DIJANGALA ENTERPRISE ƊIN da take ta koɗa mana. Mama Iman tace ok Insha Allah zanzo da shi. Shamaki ya numfasa tare da faɗin Allah ka bamu mafita. Cike da sarewar gwiwa da kuma addu'a Allah ya fidda shi. Ya nufi gida. Kafin ya kai an kira Isha'i ya isa suna raka'ar ƙarshe, ya shiga ya suka ƙarasa sannan ya ɗora, ya fito ya tarar da mutane suna kjranshi kamar kullum. Ya na ta sallamar su har Buhari masinjan Ofishin A'isha Maman Afra ya miƙo mishi takardun masu kayan ɗaki. Ya amsa ya ce Malam Buhari zan duba a gida. Gobe sai kamin bayani. Malam Buhari ya ce akwai na Ujila a ciki wannan na saman tace ba su bi ƙa'idar kawowa ba, amma mabuƙata ne in da hali ka saka hannu kai da Hajiya ita dai ta saka. Yace to ba damuwa zamu yi magana da Hajiyar. Ya gama sallamar kowa sannan ya nufi gurin Hajiyar. tana jan carbi ya zauna gefe kafin ta kammala. Ya ɗauki takardar saman da aka ce ta gaggawa ce yana dubawa. Zai iya taimakon Yarinyar ko dan sunan Babynsa da take da shi, ya ɗarsa hakan a zuciyar sa. Maimaita Rabi Abubakar, bai san sunan mahaifin ta ba, amma yasan da wahala su zo neman taimako domin ya kula cewa mahaifin Baby mutum ne mai wadatar zuci. zuciyar shi ta kasa nutsuwa ya gangara can ƙasa gurin lambar waya ya duba lambobin da kyau, gaban shi ya faɗi, ya ciro yawa yana soma saka lambar sai ga sunan da ya sawa Baby ya fito. Soyayyata. Baya buƙatar sake sanin wata hujja iya wannan ta wadatar. Ya zare takardar ya aje gefe domin gagarumar matsala ce in har Hajiya ta ga wannan takardar, sannan ya ci gaba da duba sauran. Hajiya ta katse shi da faɗin "An shigo?" Ya dube ta da sauri na shigo sannunku da gida, ya gaishe ta cikin girmamawa ta amsa tare da tambayar kasuwa, ya ce Alhamdulillah. Sai kurum ya ji kamar daga sama ta ce "Ya kabaro 'yan uwannaka?" Ya zaro ido tare da faɗin na'am. Ta share zance da kallon takardun hannunsa, "Waɗannan kuma na menene?" Ya Kalli takardun cikin sanyin jiki tare da zargin wata cikin yan uwan nasa kenan harta sanar da Hajiya ko kuwa dai Hajiyar ce da kanta ta gano cewa sun yi zaman to ta yaya zata gano hakan. Yace, na masu buƙatar kayan ɗaki ne. "Wancan fa da ka aje gefe?" Yawun bakinsa ya tsaya cak, ya hura iska tare da ajiyar zuciya, takardar wasu ne da Maman Afra ta ce ba su cike ƙa'ida ba, na sakasu a gefe ne domin sai mun kammala da waɗannan. Ta tsura mishi ido. Wace number ka ɗauka a takardar?" Zufa ta karyo mishi cikin sauri yace ta Maman Afra Anty A'isha. ,ta ce in kirata inji Malam Buhari da ya kawo saƙon,to naji ƙiwar in tsaya binciko lambar ta a waya ta sai na ɗauka a nan. Ta saki ɗan murmushi mai sauti. "Kenan ita bata samu zuwa zaman ba?" A ina? Ya tambaya da sauri. dai dai lokacin da Juma ta shigo da sallama. Hajiyar ce ta amsa domin shi ya suma da mamaki gami da fargaba. "Juma tana gaida kai tunanin me kake yi ne?" Ta katse shi. Banji ba ne Juma sannu da ƙoƙari. Juma tace ina amsawa, hidima ta zo ai dole abubuwa sun yi yawa. Yace Ummm haka ne. Ya soma kiran layin A'isha. Ta ɗaga. Ya ce Maman Afra kina jina kuna lafiya? Tace lafiya lau,yace Malam Buhari ya kawo saƙo ya ce min kin sako wani Form na Ujila kuma kince muyi waya. Tace "Haka ne." To amma kinsan dai abin nan komai a tsare yake, zan maido miki ki aje shi su jira kamar yadda sauran mutanen suke bin layi, inhar muka fara irin haka za su iya sanar da wasu cewa mun basu agajin gaggawa kuma sai ki ga mutane sun fara zuwa irin wannan roƙon,ke kanki sai su ɓata miki tsari. Tace haka ne, kuma suma mutanen basu dawo ba, munyi da su zasu zo da mahaifin yarinyar yau amma shiru. Domin masu kawo takardar sunce marainiya ce, ita kuma takardar ta nuna cewa marasa ƙarfi ne. In sunzo sai a faɗa musu su jira, sai a saka su a jerin wani watan ko?" Yace haka ya yi suka yi sallama ya ɗago kai ya kalli Hajiya wadda ke faɗawa Azima abinda zata zuba mata daga jerin abincin da Juma ta jere. Yace Naman Afra tace a gaishe ku. "Muna amsawa, ta faɗa ba tare da ta kalli gurin da yake ba. Azima tace Yaya Shamaki me za a zuba maka?" Barshi Azima sai anjima bani dai robar ruwan can. Ta miƙo masa tare da faɗin "Kamar ya yi sanyi da yawa." Hajiya tace Kije ki ci abinci zai fi buƙatar mai sanyin domin naga kamar ya yi zufa. Shamaki yace ai kuma yau ba zafi kuma ga AC ma. Tayi murmushi mai sauti. Ya san wannan murmushin na Hajiya na tuhuma ne. Ya soma tunanin yadda zai ƙoƙarta a bagarar da maganar, ya san Hajiya tana son ƙure shine. Ya miƙe bari inje inɗan watsa ruwa. Tace to babu laifi. Ya kwashi fayal fayal ɗin. Sai tace "Ajiye su zan duba." Duk da faɗuwar da gaban shi yayi sai yace to,ya ɗan sake su kan ya kai ƙasa suka tarwatse, sai ya tattara ya haɗa su ya saka na su Baby a tsakiya. Ya tafi yana shiga ɗaki ya soma faɗin Innalillahi wa'inna ilaihirra un. Ya zauna bakin gado ya ɗauki waya da sauri ya kira layin Maman Umar yace maman Umar wai in tambaye ki. Tace "Injinka." Waya sanar da Hajiya mun zauna Meeting? " Tasani! Na shiga uku?" Ta tambaya cikin gaggawa kuma atsorace. Yace yanzu na zillo daga falon nata kuma taƙi faɗa min ya akayi ta sani,na ruɗe fa ko dai acikin su Maman Nana akwai wadda ta yi subul da baki? Maman Umar ta ce babu,duk cikinmu Maman Afra ce kawai ta tafi, su gasunan kuma itama wallahi baza ta sanar da Hajiya ba. Yace to yanzu me zance mata tunda dole in koma yanzu dan akwai wata damuwar wadda tafi wannan ɗaga hankali. "Wacece ?" Ta tambaya cikin sauri. Baya buƙatar su sani dan haka ya ce ki share kawai, amma wallahi kamar in nutse bana cikin natsuwa yanzu haka. Tace kawai ka nutsu in zaka koma ka tanaji wata.maganar ko labari ɗankko mata zancan masoyinta wannan zai ɗauke mata hankali har mu tattauna yadda a kayi ta sani. Yace shike nan. Ya watsa ruwa cikin ƙarfin hali, ya saka Jallabiya mai gajeren hannu sanan ya fita zuwa gurin. Hajiya ta gama cin abinci tana shan shayi ya zauna idanun shi suna kan fayal ɗin, har yanzu suna inda ya barsu. Ya ɗarsa a zuciyarsa cewa har Hajiya ta gama dubawa ne ta ajiye ko kuwa dai dama shine ya ke tsorata kansa. Na gama tsifar kai na ce Jamila don Allah ki je gidansu Anty mai Saloon ki ce zan zo wankin kai, kuma ina son aja min gashi ance ɗari huɗu ne. Jamila ta kalli Umma ta ce Umma a tambayo? Umma tace dan Allah ku rabu da ni, ki ɗauka a cikin dubu ukunki da saurayin naki ya baki ta walima nace Umma zanyi girki walima da cincin tunda ga lemo. Jamila tace Meat pie ake yi fa ko dounot. Umma tace, duk abinda zata yi ma dai ga su can ta ɗauka, amma ki sani dai baza a yi girki ba, ana ta neman yadda za a yi a samu shi kafar a abinci biki za a haɗa a samu a fita kunya. Ga maganar kayan ɗaki Abbanku ya ƙi sam ya rubure ga maƙota sun saka ido suga nuni kunya a samu na yarda min magana. Nace Umma tunda Abba baya so kawai a haƙura da maganar Neman taimakon nan, tunda ai shi Yayan yace baya da matsala dan ba a min kayan ɗaki ba. Umma tace, " Aike sam baki da hankali musamman yanzu tunda ki ka samu wannan saurayin tashe rashin kunyar ki ta bayyana damuwar ki a kai ki, za a kai ki ba dai namiji ba. Kuma ki kasa kunne ki jini sosai wannan zaƙuwar da kike nunawa in baƙi suka zo 'yan biki ki ka sake ki ka yimin wannan giggiwar sai na saɓa miki, kayan ɗaki kuma inma ba a yi ba koda naji haushi na banza ke za a yiwa gori. Nace to Umma kiyi haƙuri Allah ya bamu mafita. Jamila ta fita domin ta tambayo min gurin wankin kai. Matar nan daƙyar ta amshi ɗari biyar wai gashina yana da cika da tsawo. Na yi mamakin ganin gashina har gadon baya matar tace wai dan ba mai na sa ba da sai ya fi haka tsawo. Nace zanzo da bikina ta sa min. Naje gidansu Umman Amina ina tambayar inda zan samu wadda ta iya Meat pie. Tace Amina ta rakani gidan wata amarya tana yi. Nan dai mukaje tace saidai taimin kwaɓi inje gidanmu in murza in soya domin mijinta zai dawo yamma ta yi. Na siyo abubuwan da ta faɗa na kwaɓi ta kwaɓamin na ɗauka mukaje Amina da Zuhra da Jamila suka tayani, na kifi ne da kayan miya dan kuɗin bazai kai insai nama ba. Muka soye shi raƙayau wai domin kar ya lalace. Na basu su 'yan tayin aiki sukace ya yi daɗi sannan na kaiwa Umma nace gashi ta ɗiba ita da Abbanmu sai a ƙulla sauran. Tace to shi saurayin naki kin ɗibar masa? Nace anan za a ɗibar masa . Umma tace "To a bari sai da sassafe yanzu dai in je in rufe. Na yi wanka na shiga ɗaki na kwanta ina ta tunanin banji muryar Mijina ba,kuma har yanzu bai ɗaga kirana ba,duk da ɗazu da safe yamin text ya ce fatan ina lafiya kuma in gaida su Umma. Na ce bari in sake kiranshi ko zai ɗaga. Jamila tace mayya sai ki yi tayi. Nace ai ko tara bata yi ba. Na danna kiran layin gabana yana faɗuwa tsabar son da nake masa ko sunan dana sa mishi a wayar na kalla sai inji tsigar jikina tana tashi. Muryata ta soma rawa lokacin da sautin muryarsa ta doki dodon kunnena. Baby Ya ku ke? Lafiya lau Yaya lafiya baka zo ba,kuma baka min waya ba, na shiga damuwa da banjika ba. Yace ayyuka na Baby suna da dama kiyi haƙuri zan zo ba na faɗa miki ba rannan nace bazan ke samun zuwa akan lokaci ba?" Nace Kasan dai alƙawari kaya ne ko? Yace "E." Na ce to ka san dai ka yi alkawarin zuwa filin saukar karatunmu domin kaga karatuna ko? Yace "Haka ne." Na ce to gobe ne da ƙarfe goma na safe za a fara, dan Allah kazo ka ga karatuna. "Wai dama gobe ne?" Ya tambaya da sauri. Nace e mana. "To kuwa gara da kika tuna min gobe Lahadi insha Allah zan samu in zo. Cikin Farin ciki nace to ka gaida Hajiya da su Anisa,kuma ina gaida su Anty su duka. Yace duk zan faɗa musu. Nace to sai da safe yace to mu kwana lafiya. Jamila ta lalle ni bayan na gama waya tace wai ke Yaya Baby har wani canza murya ki ke yi ba in zakiyi waya da Ya'yan nan, sanan wannan wayar taki ba a saka mata kati ne? Tunda aka baki ban taɓa jin kice a siyo miki kati ba, kuma rannan har Baabar Kurna ki ka kirawa Umma, sun jima suna magana. Sai lokacin na kula da haka na ce taɓ tun katin da ya kawo a kwalin wayar kuma ai katin ɗari biyar ne. Jamila tace duba Balance ɗinki mu gani, na tsurawa lambobin ido baya na danna bangane adadin kuɗin ba. Na furta ina kallon Jamila. Tace, mu gani tace kamar ɗari takwas ko dubu takwas. Nace ko dai naira takwas ba. Muka sa dariya. Nace duk tsiyarsu ko nawa ne dai sai sun ƙare domin kirana zantayi ƙila kuma ina cikin wani tsari ne wanda suke bada bananza. Jamila Tace 'hakane ma. Na sauke ajiyar zuciya na ce Allah na gode maka Ubangiji kamin komai. Jamila tace Yaya Baby kina bani mamaki har cikin dare ina jinki kina yiwa Allah irin wannan godiyar, wallahi ba su Umma ba ko ni ina jin haushin yadda kika koma mara kunya lokaci guda. Na tausasa Murya yanzu wannan rashin kunya ce Jamila yi wa Allah godiya? Tace "Ai ba iyaka godiyar zaki tsaya ba, da banyi magana ba cewa zakiyi da ya baƙi miji kamar Yaya Aliyu a dai-dai wannan lokacin." Nace to Jamila meye laifin hakan kar ki manta a da fa ko kare bai ce yana sona ba har tsegumina ake a layi yanzu kuwa an dawo masu zaginma sai shige min suke yi. Jamila tace to ai shigewar ta munafirci ce, in kin yarda, ɗazu da Umma tace in amshi rariyar da Umman su Nabila suka ara a gidan na samu Umman su Fati mai awwara,tun daga soro naji suna cewa wai ba'a san asalin Yaya Aliyu ba,babu bincike daga zuwa an ɗau yarinya za a bashi. Wai ƙilama ba ɗan ƙasa bane ƙarshe sai kin tara 'ya'ya ya gudu ya barki. Umman Fati ce da wannan dogon jawabin. Umman Nabila kuwa tace su suka sani dubi uban kayan lefe gashi sun saka aure da gaggawa kamar suna da wata tsiya ma ji ma gani dai mu 'yan rakiya ne har gidan ango muga abinda zasu kai mata." Nace Muna fukai ina son mijina haka, ko daga sama ya faɗo, kinsa Allah da nice naje sai na zage su, nifa Jamila akan Aliyu iyayena ne kawai suka fimin shi sai ku ƙanne na. Jamila tace shiga nayi da sallama sai suka hau borin kunya na amso na dawo ko Umma ban faɗa mata ba. Nace Yawwa gara kar ki faɗa mata dama, cikin damuwa take. Ai basu kaɗaiba ko gidansu Zuhra da suke 'yan uwanmu ai suna nuna baƙin cikin su. Kuma suma suna munafircin Yaya Aliyu na maganar bincike shiyasa ban so aka ƙara sati ɗayan nan ba wallahi. Domin gani nake wani zai iya zuga su Umma su ce sun fasa bashi ni. Jamila ta ja tsaki ta kwanta tare da faɗin ni fatana Allah ya sa yana miki irin son da ki ke masa." Nace yanzu har Kinji haushi kenan? Ta ce "Zakewar taki ce tana yawa, kuma kisan Allah Umma da Abba abin yana basu takaici kyazo kija wa kanki suce sun fasa mugani ko zaki bishi ba aure. Na ɗora kaina a gadon bayanta ina faɗin bazan bishi ba Jamila, amma na tabbatar zan mutu. Dakin yayi tsit Jamila haushi ya hana ta bani amsa. Ni kuma na faɗa tunani wai ace an fasa. Da sauri naga Jamila ta tashi zaune tasa hannu biyu ta tallafi fuskata wai ashe hawayena ne suke sauka a gefen cikinta. Tace Kuka ki ke Yaya Baby, me akayi na kuka?" Na sauke ajiyar zuciya cikin rawar murya nace wallahi ban sani ba Jamila, amma na samu kaina a matsananci son Yaya Aliyu iya tunanin sa in na zurfafa sai na yi wannan kukan. Kuma na kasa gane dalili. Kimin fatan Allah ya sa shima yana sona. Jamila ta shiga lallashina tana share min hawaye tana faɗa min cewa tabbas ya na sona, kuma aure babu fashi kuma za a yi komai cikin rufin asiri. Muka kwanta cikin saƙe saƙen zukata. Sai Muryar Abba muka ji yace "Ke Baby zo nan.'.. Muka tashi da sauri zaune nace Jamila me yafaru? Ta yarfa hannuwa alamun bata sani ba. Jikina ya soma ɓari, na ce kodai ya ji zantukamu ko kuma wasu sun shigo shi akan maganar binciken Aliyu ya fasa aura min shi. "Ina ki ke?" Muryar shi ta ƙara ratsowa. Jamila cikin sauri tace kije mana amma komai zai ce ki yi shiru. Na miƙe na fita yana zaune kan tabarma inda sukan zauna da Umma. Shamaki ya buɗe flas ɗin abinci ya soma zuba farar shinkafa, idanun Hajiya suna kansa har ya gama sannan ya zauna ya fara ci yana son tuno wane labari ne Hajiyar ta fi maida hankali sosai. Kodai labarin mahaifin su,ko kuma dai labarin kasuwancin su daidai lokacin wayar shi ta soma ruri, ya kalla Soyayyata . Ya ɗago ido ya kalli Hajiya ta tsare shi da kallon tuhuma dole ya yi wayar a gabanta domin fidda kansa. Ya yi ɗan murmushi bayan ya gama wayar ya tauna abincin da ya zuba a bakinsa zai yi magana,sai ta ɗaga masa hannu, gama cin abinci, ka fi kowa sanin cewa bana son ana magana lokacin cin abinci, ka gama sai kamin bayani kamar haka.. Duk saboda son yarinyar ne ka soma munafurta ta har ka shirya zama da 'yan uwanka saboda ni? Sannan ka ciro min fayal ɗin da kake ɓoyewa da hannunka har kana zubar da su dan kawai in rasa gane wanene ka aje gefe. Sannan ka min bayanin dalilin yin duk wannan alamun na rashin gaskiya da kake yi tun da ka shigo gida, kuma ka faɗa min da wa ka yi waya da ka shiga ɗaki! Cokalin da ke hannun Shamaki ya faɗi abincin ya zube masa a riga. Yawun bakinsa ya ƙafe sannan ya tsaida idanun sa akan Hajiya cikin tsananin firgici. 🖊️🖊️🖊 ️*HAMSHAƘIYAR UWA🧕🏻* *NA* *HALIMA ABDULLAHI K/ MASHI* _PAID BOOK_ _Kuɗin karatu ₦600_ _Account number 0700549935 Halima Abdullahi Access Bank a turo shaidar biya ta wannan number 08140004302 ko katin Mtn_ _Phone 08140004302_ *DOKA* _Ban amince wani ya ɗora littafin nan a wani Social media ba,ko a maida mini shi Audio ba tare da iznina ba yin haka daidai yake da fuskantar fushin hukuma. A kiyaye_ *Masu son a Tallata masu hajarsu suyi magana ta wannan number 09068032427* *Page 12* Na isa gaban Abba cikin tsoro na zauna, duk jikina babu inda baya rawa, ina da tabbacin da "Abba zai ce an fasa ba Yaya Aliyu ni, bana ko shakka zan iya faɗuwa a gurin sumammiya. Sai naji ya tausasa murya ya ce "Baby" Cikin rawar murya na ce na'amm Abba. Yace "Kina ganin baki da wata damuwa in har aka ɗaura auren nan aka kai ki gidan yaron nan a haka babu kaya ko kuwa kina ga akwai wata damuwa in roƙe shi ya ɗan ƙara mana lokaci muga abinda Allah zai yi?" Na sauke wata wawiyar ajiyar zuciya. Sannan nace Abba ba ni da wata damuwa akan haka, ai munyi maganar da shi ya ce ai duk al'ada ce, kuma ya ce min zai siya in ya samu kuɗi. Abba ya daka min tsawa "Ke! ni ban tambaye ki dogon labari ba, abin da na tambaye ki kawai shine, zaki zauna da mijinki lafiya ko da ba mu samu munyi miki kayan ɗaki ba?" Zan zauna. Na bashi amsa da sauri kamar ina jiran tambayar. Umma ta fito daga ɗaki tace Sannu Baban Babu nifa gaskiya bazan iya kai yarinyar nan gidan miji babu kayan ɗaki ba, kodai ka je ka ciyo ko bashi, ko kuma ka yarda muje ka saka hannu a wancan na tallafin a karɓo, baka da shi, to menene naka na yin girman kai? Abba ya miƙe "Salamatu" ya nuna Umma da yatsa cikin tsananin fushi wanda ban taɓa gani ba, yace ki shiga hankalin ki da ni, in ba haka ba kuma zan yi matuƙar baki mamaki domin zaki tafi gidanku ki haihu a can , ni kuma in aurar da 'yata cikin kwanciyar hankali. Jamila ta fito da sauri ta nufi gurin Umma ta riƙe mata hannu ta na cewa "Umma kiyi shiru: don Allah. Ni kuma kuka ne ya suɓuce min na kasa furta komai, saboda ni iyayena suna sa in sa abinda ban taɓa gani ba tunda na ta so. Kamata ya yi ince su yi haƙuri na fasa auren ma gaba daya, amma yadda nake ji koda tafiya Umman zata yi ba zan iya furta hakan ba, shin dama haka son yake ? Da numfashi yake kamar wani bala'i ko kuwa nawa son ne ya zo a haka? Muryar Umma ta katseni. Lallai Abubakar Allah ya kawo mu lokacin zaka faɗi haka tsakanin ni da kai, to ni kuma da inga aure nan a haka gara ayin bana gidan nan, na yarda da haka. Amma in ka tashi ka bani saki uku ras yadda ba sai na dawo ba.. Da sauri nace Umma kuyi haƙuri saboda ni ba zaku rabu ba. Ni gaba ɗaya ma na fasa au! au!! Sai na samu kaina da kokowa da numfashi na matsawar na furta kalmar zan iya mutuwa. Jina nayi na kai ƙasa ina wani irin numfashi, ina ta kuma ƙoƙarain furta na fasa auren kuma ina jin salatin iyayena kamar daga can nesa, sannan ga muryar Jamila tana kiran yaya Baby! Zuwa can kuma sai na daina jin komai. A dai dai wannan lokacin Hajiya ta kalli Shamaki sosai zarginta game da takardar ya bayyana kuma in har haka ne yarinyar sun zo, neman taimako ne haƙiƙa sun fadi babbar jarabawar ta. Wanda hakan zai sa ko da an yi wannan auren to sun zaɓtarewa yar su wani babban maki. "Ka bani in duba" ta furta cikin isa irin yadda take yi in ƙasaitarta ta motsa. Bashi da wani zaɓin da ya wuce ya bata waɗannan takardun na gaskiya ya saurari Allah wanda yake ta kira sunayen shi ɗari ba ɗaya a ƙasan zuciyarsa. Sanin kanshi ne in ya bata waɗanda ba su bane zata gano na gaskiya ta hanyar yin magana da Maman Afra. Wanda hakan zai iya haifar da ƙatuwar matsalar da zata iya soke auren Baby wanda yake ayyana hakan da mutuwar tsaye a wurinsa. "In har ka bari na tafi daga falon nan karka sake ka tambayi dalilin da ya sa na janye batun auren ka." Kalaman Hajiya suka ratsa kunnuwansa. Cikin sauri ya miƙa mata tare da faɗin afwan afwan ina duba shi ne. Ta amsa tare da faɗin "Ai guda ɗari ne a gurin dole ka kasa tantancewa. Ta ɗauki gilashinta ta saka ta soma bin shafi shafi tana dubawa, bata ga wani abu da zai sashi yin irin wannan rashin natsuwar da har ta jefa shi a zarginta ba, amma dai ta yi imani dole akwai wani abu. Don haka ta maida hankali ga Number daya ɗauka, yana kallon ta har ya soma murna, sai kuma ya zaro idanu ganin tana ɗaukar lamba. Ta danna kira ya tafi, har ya katse ba a ɗaga ba.Ya haɗiye yawun bakin sa da ya ɗauke, sai kuma ya ga ta ƙara dannawa. Sai aka ɗauka, ta danna handsfree ta yi sallama, cikin yanayin damuwa aka amsa. Tace "Daga Zeena Foundation ne inda kuka zo neman taimako, ance ku kawo mahaifin yarinyar amma ba ku zo ba?" Cikin girmamawa aka bata amsa, "Kiyi Haƙuri Hajiya Mahaifinta ya ce shi ba zai zo ba." Kafin ta ƙara magana sai taji muryar namiji ya amshi wayar. yana magana cikin fushi, Hajiya yarinyar nan tawa ce dan ina talaka bani da rashin godiyar Allahn da har sai naje maular kayan ɗaki. Batare da izinina taje ba. Kuma ban aike ta ba, bana buƙata kiyi haƙuri. Hajiya zan mata iya yi na, ku ba waɗanda suka fini buƙata." Ya kashe wayar ba tare da jiran amsar ta ba. Falon ya yi tsit in bada ƙaran AC da kuma TV da ke yi can ƙasa. Kusan daƙuƙa tamanin, sannan Hajiya numfasa ta ce, "To kaji sirikin ka irin amsar da ya bayar." Shamaki yace Sirikina kuma Hajiya? Tace "Ka dai na yi kamar wani baka gane komai ba, tun daga sunan yarinyar na fuskanci surukan ka ne, kana son ka ɓoye min domin kar in gani, dama baka ɓoye kana nuna rashin nutsuwa ba, babu lallai in gane abinda ka ke ciki. Ta gyara zama ta ɗanyi ƙasa da murya, tace, In tambaye ka mana Shamaki." Ya sunkuyar da kai tare da faɗin ina jinku Hajiya. Tace "Wai inada wani mugun hali ne? Da sauri yace Subhanallah! Mai ya kawo wannan furucin! Baki da mugun hali Hajiya, baki kusanci, mugunta ba. Tace "To me yasa ka ɓoye min cewa surukan ka sun zo neman taimako?" Ya numfasa Wallahi Hajiya zaman da nayi a nan gurin shine ya kawo har na na kula. Sannan na ɗauki lambar ne na bincika na gano. "To daka gano da wane irin hukunci zaka ɗauka?" Dama dai zan maida ne su bi ƙa'ida da ake bi, domin abu bai min daɗi ba, yadda nasan mahaifin yarinyar nan da haƙuri wadatar zuci da ƙoƙarin nema kuma ace sun zo neman taimako. Wallahi da kika kira shi naji daɗi sosai da naji cewa babu sa hannunsa, ita ma Umman ta su ƙila wasu ne suka zugata. Hajiya ta sauke ajiya zuciya tace "Ni kaina da ace Uban ya zo haƙiƙa sun kayar da 'yar su babbar jarabawa. Amma me zaka ce game da ita uwar da take aikata abu ba tare da sanin mijinta ba, wane tunani zaka yi game da 'yarta mai kwaikwayo daga gareta? Kasan dai uwa ce makarantar farko a gurin kowane yaro." A ƙasan zuciyarsa yace ta ƙirƙiro wata damuwar Allah ka fidda ni. Ya ɗanyi gyaran murya yace Hajiya ba wannan ne abin dubawa ba, abin dubawa shine, da Abba ya ji abinda Umma ta yi kuma ya daka tsawa, ya hana kuma akaji ba a bijire ba. Shine abinda za ku duba Hajiya saboda wancan kuskuren ne da kowa zai iya aikatawa. Ko Allah da ya halicce mu muna yi masa kuskure amma da mun amshi kuskurenmu mun tuba shike nan. Hajiya ta saki maganar da faɗin "To ko ba komai sai ka godewa sirikin ka domin yadda ya yi jarumtar ƙin amsar kayan nan, ya kwace ka daga ƙaryar da kamin ta farko, sai dai kuma bayan tiya akwai wata caca." Shamaki ya zaro ido. Wacce fa? Hajiya tace "Wannan zan jira sai lokacin da ka ke jin cewa ni mahaifiyar ka ce, kuma wadda ta ke yi maka so da ƙauna zalla babu sirki, wadda ko mutum ka kashe zata iya rufa maka asirin da har duniya ta tashi ba wanda zai ji. Kai wadda zata iya bada ranta domin fansar naka. Lokacin da duk ka fahimci hakan sai mu yi ɗaya magana." 🖊️🖊️🖊️ *HAMSHAƘIYAR UWA🧕🏻* *NA* *HALIMA ABDULLAHI K/ MASHI* _PAID BOOK_ _Kuɗin karatu ₦600_ _Account number 0700549935 Halima Abdullahi Access Bank a turo shaidar biya ta wannan number 08140004302 ko katin Mtn_ _Phone 08140004302_ *DOKA* _Ban amince wani ya ɗora littafin nan a wani Social media ba,ko a maida mini shi Audio ba tare da iznina ba yin haka daidai yake da fuskantar fushin hukuma. A kiyaye_ *Masu son a Tallata masu hajarsu suyi magana ta wannan number 09068032427* *Page 13* Cikin sanyin jiki Shamaki ya sunkuyar da kai, tabbas ya sani Hajiya tana yi masa so tsantsan na tsakanin ɗa da mahaifiya. Kuma tabbas 'yan uwansa suna son sa sai dai fa ba kamar Hajiya ba. Kuma su suna iya tattauna damuwar shi da mazajensu saboda so da kuma yarda da juna. Amma Hajiya bazata iya tauna kowace matsala tasa ko ƙarama ko babba da su 'yan uwansa ba. Hajiya ce keda maganin damuwar sa kuma ita yafi dacewa ya kai ma wa kuka, kamar haka ta ke nufi. Ya ɗago ya kalleta ta zubawa TV ido, kamar tana kallo, amma ko shi ya san tunani kawai take yi. Ya ɗan ƙara matsawa kusa. A hankali ya furta "Hajiya" ta yi kamar bata ji ba. Ya sake matsawa kusa da ƙafarta, yace Hajiya. "Faɗi ina ji." Ta furta ba tare da ta waiwayo ba. Yace tun tuni nasan kina min so fiye da irin wanda ki ka furta. Ba zan iya kawo bayanin irin soyayyar da kike min ba, ni da 'yan uwana. Haƙiƙa na samu 'yan uwana mu yi magana, amma ba kamar yadda ku ke zato bane Hajiya. Nauyi nike ji in sameki da irin wannan zancan. Hajiya ta maido kallon ta gare shi, ta soma faɗin "Ni fa na ɗauki cikin ka, na haifeka, na shayar da kai da wannan maman nawa, ni ce wadda na riƙe ka aka yi maka kaciya. Aliyu ka tuna ban daina yi maka wanka ba sai da na ga alamun balaga sun fara bayyana atare da kai. Lokacin ka shiga ajin farko na ƙaramar Sakandire. Anyi haka? Shamaki ya kaɗa kai alamun ya tuna. Tace "To a kanme har zaka ce kana jin nauyi na?" Shamaki cikin tsananin kaunar mahaifiyar sa ya ce, Hajiya na yi kuskure mai girma, kece ya kamata in tunkara amma ki yafe min tare da sauran 'yan uwana a ƙoƙarin su na nuna ƙaunarsu a gare ni, amma ko da na faɗa musu duk sunce gurinki za a dawo sai dai su za su zo a madadi na. Hajiya tace a a bana bukatar su a gidana game da wata matsala taka. Ni da kai muna kwana a gida daya su da ke kwana a gidan mazajen su shine har sai sun wanko ƙafa domin yin gyara a matsalar gidana?" Ayi mana afwa Hajiya, zan sanar da su ba sai sun zo ba. Kuma insha Allahu zan sanar da ku damuwar a yanzun nan in har kun yi min izni. Hajiya ta share kamar bata son ji har da cewa "Yau ka canza mana tsari, har lokacin bacci ya kusa ba muyi abinda ya kamata .ba." Shamaki yace insha Allahu za mu fidda komai kafin mu kwanta. Sannan ya sake marairaice murya in faɗa Hajiya?" Ta tattara hankalinta gare shi "Faɗi ina ji amma da sharaɗi, ko ka faɗamin koma menene, bana buƙatar ka fara roƙo na in amince da buƙatarka." Yaɗan yi shiru. Tace Inhar haka zaka yi to ina son ka bar zancanka. Sai yanzu ya fahimci gaba ɗaya Hajiya batasan komai ba tsabar lissafi ne kawai ta rikitashi ga shi har ta yi nasarar tarfashi zai faɗa mata, ƙila in da abinda ta sani bai wuce tasan ya je gidan Maman Umar shida sauran 'yan uwansa ba. Ya dube ta ta kafe shi da ido. Ya sunkuyar da kai, yace Wai Hajiya wa ya faɗa miki cewa mun haɗu da su 'yan uwana? Tayi ɗan murmushi mai sauti. Ta fahimci ya gano shurinsa ta ke yi bata da masaniyar komai. Ta ɗaure fuska. " Sai ana magana ka sauka daga kan layi kasan da lokacin bacci na ya yi zan miƙe kira min Azima ta shafa min maganin ƙafa. Yace to Hajiya bari mu gama maganar, dama fa kan batun girki ne na ranar taron ki da amarya ke yi, sai kuma maganar budurci. Ya ɗanyi shiru ko zata ce wani abu amma bai ji ta ce komai ba, dan haka ya ɗago kai ya dube ta. Shi take kallo har lokacin. Ya ci gaba, saboda ita Baby 'yar talakawa ce ba lallai ta iya girkin zamani ba,, a taimaka a sa su Juma.. Ta ɗaga mishi hannu. "Na taɓa cewa ga kalar girki da Amaryarka za ta yi?" Ya girgiza kai. Tace to "Wannan ban karɓa ba,ta zo ta dafa irin wanda ta iya na gidan nasu ta bamu muci, anrufe wannan batun sai kuma wanne ka ce?" Ya haɗiye yawu maganar budurci ne ce kawai duk yadda tazo bama sai mun tattauna maganar ba. Saboda likitoci suna ta bayani shine har Maman Afra take bada misali da matsalar Afra ta kwanaki. Hajiya ta ɗaga masa hannu, bana son wannan maganar ka barni akan ra'ayina. Yayi ɗif domin ta rufe ƙofar magiya tun farko, dan haka ya ɗakko ƙaramar laptop ɗinsa dake gefe a jaka zai fara yi mata bayanin kasuwa. Azima ta shigo da sallama ta tambayi Hajiya cewa a fara shafa magani yanzu? Hajiya ta yi mata izni. Na farka na ganni kwance kayana a jiƙe sharkaf kaina a cinyar Umma, ga Abba na min fifita. Ajiyar zuciya irinta masu kuka na ji Jamila na yi, na tashi zaune da sauri nace Umma menene? Sai naji gaba ɗayansu suna min sannu, na tuna me yafaru. Da sauri nace Dan Allah Umma ban taɓa gani kuna faɗ ba sai a kai na. Na soma kuka, Abba ya ce ke komai ya wuce kar kiyi kuka. Umma tace ba inda ke miki ciwo? Na girgiza kai alamun babu. Umma Ta ce "To miƙe kije ki cire kayan." Na tashi Jamila ta zo da sauri ta riƙe min hannu muka nufi ɗakinmu, ina jin Abba yana lallashin Umma wai ita ma ta tashi taje ta kwanta. A ɗaki na tambayi Jamila ko na yi Alhaji ne. Tace suma na yi Lokacin da nake ƙoƙarin furta cewa na fasa auren Aliyu." Nace iko Allah ni wannan wane irin so ne nake masa?Jamila tace Abba da Umma jikinsu ya yi sanyi da wannan son da ki ke masa. Abba ya ce gara kawai a ɗaura a kai ki. Wani daɗi naji a zuciya ta, na ɗakko Al'ƙur'ani na ce bari in sake jaddada karatuna gobe a gabansa zan yi ina son in burge shi sosai. Gashi na ci Sa'a ina daga cikin ɗalibai mu uku da Malam ya ware zamu yi karatu mu kaɗai kuma biyun maza ne ni kaɗaice mace. Jamila tace kinsan kina da muryar ƙira'a ne sosai Yaya Baby. Nace na sani 'yan ajinmu sai suce wai ina shan na'a na'a ne. Jamila tace "Baiwa ce. Haka na shiga raira karatu muryata tana ratsa tsakar gidanmu ko ina ya yi tsit. Na tabbata iyayena suna alfahari da ni in suka ji ina rero karatun Kur'ani. Washegari tun daga sallar asbashi ban koma ba, kafin bakwai tuni na gama shiri na sha atamfarmu ta anko da sabon hijabi, Umma tace in ɗauki takalmi a cikin kayan lefena in saka. Na gama shiri tsaf sannan na zauna na rubutawa Shamaki saƙo kamar haka.. Sanyin zuciyata fatan ka tashi lafiya tare da dukkan yaran mu da kuma Hajiyata. Dan Allah ina ƙara tunasar da kai cewa yau ne saukarmu zuwanka ya fi komai mahimmanci a guri na. Ina saka ido. Bayan na tura na jira amsar shi, amma bai aiko min ba, na kira layin naji yana waya. Ance ƙarfe takwas ta yi mana a makaranta amma ni harda minti goma, gaba ɗaya duniya ta daina min daɗi bani da tabbacin zuwan masoyina. Har Jamila ta fahimta ta tambaye ni,na faɗa mata damuwata. Ta shiga lallashina akan tasan zai zo, kawai dai wani abin yake yi bai amsa kira na ba. Nace amma ai nayi masa saƙo sai ya bani amsa. Jamila dai ta shiga lallaɓani, muka tafi gurin sauka. Fili ya cika tantsam Malaminmu ya nuna min ajin da aka ware mana mu 'yan sauka, na shiga dukkan masu saukar sun hallara kowa na cikin farin ciki masu hoto suna ta ɗauka. Na samu guri na zauna, Fatima Shu'aibu ta kalle ni. tace "Lafiya kuwa Rabi'a Abubakar naganki shiru. Na yi ɗan tsaki tare da faɗin ba komai. Na ƙaƙaro ɗan murmushi Malam Awwal ya ce za a bar Mutum uku su yi karatu ɗaiɗaya ya faɗi suna? Na tambaye ta cikin sanyin jiki. Fatima tace "A'a, amma dai nasan kina ciki. Nace ba lallai bane. Ina rufe baki yana shigowa. Ya ƙara tunatar da mu yadda zamu natsu sosai a gurin karatu da kuma yadda zamu fito cikin tsari. Sannan ya kira sunan maza biyu, Aminu Sani da Ashiru Ya'u. Suka fito, ya dube su yace akwai ta ukun ku ita ce Rabi'atu Abubakar na tashi da sauri na fita domin nasan cewa ina cikin waɗanda za a sa su yi karatu ɗaiɗaya, makarantarmu suna ji da muryata a ƙira a. Malam ya ce ku ukunnan kune zaku yi karatu, kuma Alhamdulillah kune kuka zo na ɗaya zuwa na uku. Dan haka ku zama cikin shiri na amsar kyautuka. Nan dai muka shiga murna duk da cewa bamu san waye zakara ba. Ni dai nasani bana wuce ta biyu ko ta uku a duk jarabawa ban taɓa yin ta ɗaya ba, yanzun ma ban yaudari kai na ba, na fi zaton ta uku. Shiko Aminu kowa yasan baya tsallake na ɗaya. Bayan an kiramu mun fita zuwa rumfar da aka tanada mana kujeru mun zauna sai na soma raba ido ina zan hango wani nawa. Na hangi .Abbanmu a rumfar iyayen yara cikin sabon yadinsa shi da Abba su Zuhra. Sannan na hangi Umma tare da wasu danginta na Kurna. Can a wata rumfar na hango Dangin mahaifina matan har da yaransu, amma damuwata ban hango masoyina ba. Duk sai naji raina yana ɓaci. Da aka fito da mu muka karanta fatiha da shafi biyu na baƙara sannan muka koma muka zauna, aka ci gaba da gabatar da abubuwa har zuwa lokacin da aka zo kan karatunmu. Ashiru aka soma kira aka ce ya zaɓi surar da ya ke son karantawa ya karanta. Ya zabi suratul Yasin. Da ya gama aka tsai da shi akan mumbari aka gabatar da shi a matsayin wanda ya zo na uku, aka bashi allonsa,sannan aka bashi kyautar sa ta musamman daga hukumar makaranta saboda taimakon Malamai gurin koyar da ɗalibai na ajin ƙasa. Sai kuma aka kira Aminu Sani cikin mamaki ya lalle ni, Nima haka domin dai na bayar ni za a kira. Shima dai bayan ya gama karatu an gabatar da shi a matsayin shugaban ɗalibai, ya kuma amshi kyautar yabawa da zuwa sahun bayan liman a lokutan salla a makarantar. Lokacin da aka kira ni sai da ta kusa sani ta taɓani domin takaicin rashin halartar Aliyu yasa komai ya saɓule min. Na tashi jiki ba ƙarfi na hau mumbari, an bani damar karanta duk surar da ta min, sai na samu kaina da karanta suratul Muhammad domin ina son ta. Ina faɗin Muhammadur Rasulullah! Sai na ji muryata ta soma rawa lokacin da na ji ɗaukacin gurin an amsa da S.A.W. Haka na kammala ciki zubda Hawayen da ba zan iya fassara dalilin zubar su ba. Guri ya ɗauki kabbara ga masu hoto da bidiyo amma babu sanyin zuciyata. Malam ya gabatar da ni a matsayin ɗalibar da ta zo ta ɗaya acikin kaf ɗaliban set uku da muka yi sauka. Sannan aka bani kyautar Shugabar ɗalubai wato Amira. Sannan aka bani kyautar ɗalibar da tafi kowace ɗaliba ladabi da biyayya ga malamai. Har zan sakko sai aka sake tsaida ni aka bani wata kyautar itama an naɗe ta, aka ce daga mijin da za a ɗaura mana aure da shi sati mai zuwa.... 🖊️🖊️🖊️ *HAMSHAƘIYAR UWA🧕🏻* *NA* *HALIMA ABDULLAHI K/ MASHI* _PAID BOOK_ _Kuɗin karatu ₦600_ _Account number 0700549935 Halima Abdullahi Access Bank a turo shaidar biya ta wannan number 08140004302 ko katin Mtn_ _Phone 08140004302_ *DOKA* _Ban amince wani ya ɗora littafin nan a wani Social media ba,ko a maida mini shi Audio ba tare da iznina ba yin haka daidai yake da fuskantar fushin hukuma. A kiyaye_ *Masu son a Tallata masu hajarsu suyi magana ta wannan number 09068032427* *Page 14* Take fuskata ta canza zuwa murmushi, na shiga kalle-kallen ko zan iya hango shi Mijina. Sai dai har na sakko Jamila ta zo da gudu ta amshi kyautukan ban hango shi ba. Daga nan sai malamai suka gabatar da asusun makaranta domin neman taimako. Kabbara da naji an ɗauka ita ce tasa na ɗago kai na dubi ta kusa da ni nace menene? Tace "Babban baƙon da aka gayyato ne ya ke jawabi cewa ya bada Miliyan uku ayi gyaran makaranta." Sai na sa hankalina a gurin ina faɗin gaskiya ya taimaka. Sai naji yana faɗin "Wannan yarinyar mai albarka Allah ya yi mata albarka tare da iyayen ta wadda ta zo ta ɗaya ga sheda da ta samu ta ladabi haƙiƙa ta zama abar alfahari ce." Sannan ya ci gaba da fadin "ina yarinyar tazo nan. " Malam ya zo da sauri ya tasani. Kyakyawan Basarake ne yana zaune cikin shigarsu ta sarakuna yasha gilashi baƙi. Na durƙusa a gabansa. Yace yarinya zaki ci gaba da karatu ne? Na zuba masa ido kenan abin nawa ya kai duk wanda ya yi magana sai inji muryar sa irin ta masoyi na. Malam yace "Aure za ayi mata ranka ya daɗe kunya ta ke ji shi yasa ta yi shiru." Ya ce "To Allah ya albarkaci auran mun zaci zakici gaba da karatu ne mu faɗa miki zamu ɗauki nauyin karatun. Amma tunda ance aure za a miki to in mahaifanki suna wannan guri muna saanar da su cewa zamu sai miki kayan ɗaki da kayan da duk wata gara. Allah miki albarka Ya sa ki yi amfani da abinda ki ka karanta, kuma muna yi miki nasiha da ki bi mijin shima ya shede ki kamar yadda ki ka samu sheda daga Malaman ki . Su kuma sauran yaran da suka ci jarabawa zamu basu dubu ɗari ɗari. Ragowar yaran da suka yi sauka kuma za su rabauta da naira dubu ashirin ashirin. Ta ke aka soma kabbara. Daɗi ya rufe ni addu'a na ke Allah ya sa ba mafarki na ke yi ba. Allah mun gode maka ya kawo mana mafita ni da iyayena. Babban baƙon shine ya miƙa mana allunanmu aka ɗauke mu hotuna. Lokacin da zai bani nawa sai na ji ya ce abar alfahari kin na tabbar mijin ki in yana nan to yana cike da farin ciki da godiya ga Allah. Na zubawa fuskarshi ido muryar Aliyu na ce. Malam ya min tsawa wai in wuce, Sannan ya basu kuɗaɗensu a Envelope ni kuma ya ce a bashi lambar wayar mahaifina. Malam ya sa lasifika ya ce in Mahaifin Rabi'atu Abubakar yana gurinan ya iso nan ana son ganin shi. Abba yazo cikin murna suka gaisa da babban baƙo yana ta godiya sannan Abba ya yi godiya ya bada lambar waya inda wani da ke tsaye da wayoyin babban baƙon ya amshi lambar ya saka a ɗaya daga cikin wayoyin. Suka tafi malamai suka raka su gurin wasu manyan motoci. Haka dai sauka ta tashi ana ta farin ciki da murna a gurin . Su Umma abin ba a magana. Ni kam tun kafin mu ƙarasa gida na amshi wayar a hannun Jamila na soma kiran layin Yaya. Na kira ya fi sau goma amma ɗan tahalikin nan bai ɗauka ba. Na ja tsaki na miƙawa Jamila wayar. Tace "Wai ke duk wannan alkhairi da ya same ki a yau amma har yanzu kina ƙunci." Nace dole in yi ƙunci baizo ba fa. Jamila tace "Ya zo mana." Cikin sauri nace kun haɗa ido? Tace "A'a amma ga kyauta ya bayar?" Nace zai iya aikowa. Nima zan fara gwada mishi nawa rashin kulawar tunda haka ya zaɓa. Jamila tace "Kamar zata iya." Nace zaki gani kuwa. Labari fa ya watsu a unguwa sai murna ake zuwa taya Ummanmu. Da dare ina jin Abba yana cewa Umma kinga dai abin Allah ko? Tace "Wallahi Ubangiji ya share mana hawaye, wannan lamari Allah muna godiya a gare ka." Muka shiga ɗakinmu. Jamila tace ki buɗe mana kyautar ango mugani mana. Na tura mata kwalin ke ki buɗe, domin ni ita kanta kyautar haushi take bani. Wani kyakkyawan siririn agogo ne mai kyau ruwan gwal, sai wani zobe kamar na azurfa yana da jan dutse shi mai kyau. Ga ƙaramin ƙur'ani mai girma izu sittin, ga kuma wani kyakkyawan carbi mai ruwan gwal. Take na ruɗe ina ɗaga kayan cikin farin ciki. Jamila ta sa dariya tare da faɗin "Kin daina jin haushin kenan?" Nace ai ba haka bane, ƙur'ani mai girma fa ya bani ya bazanyi murna ba. Haka dai har muka kwanta ban samu wani kira ko saƙo daga mijin da zan aura ba. Hajiya ta fito daga cikin ɗakinta ƙarfe uku na rana taɗan matse bacci kafin la'asar. Idanunta suka sauka akan yaranta sun baje a falonta suna ta hira, ga alamu sun gama cin abinci domin Juma tana ta gyaran gurin. Duk suka miƙe suna yi mata sannu da fitowa. Ta amsa musu bayan ta zauna, tace "Ashe kun jima kuna jirana, yau wani bacci na ji tun da nayi azahar na shiga ciki. Maman Nana tace Ai kuna shiga ciki na iso, Juma ke faɗa min sai kuma ga su suma. Hajiya ta kaɗa kai cikin isa Tace "Marabanku da zuwa suka amsa. Ta kalli wasu lesuka dake zube kan kujera, tace muga kayan can na waye?" Maman Iman tace nawa ne siya na yi zan baiwa Ango shine aka ce tuni an kai lefen. Shine zan ɗinke kayana. Hajiya ta ciro daga leda ta taɓa jikin leshin. "Ina kika samu wannan leshin kayan London ne ko har can ki kayi Oder?" Maman Iman Tace 'a'a akwai DIJANGALA ENTERPRISE sune suke shigo da su, kayan su suna da kyau kuma Hajiya ga ta da farashi Hajiya tace "Mace ce mai kamfanin?" Hajiya ta tambaya tana ƙara taɓa jikin leshin. Maman Umar tace E, mace ce. Hajiya ta gyaɗa kai tare da faɗin Allah ya dafa mata. Ina son inga mata suna dagewa da kasuwanci, ki duba min lafaya irin waɗanda kika san ina so kamar kala goma sai ki turomin. Maman Umar tace bamu da su a kasuwa ne?" Hajiya tace "Karfafa mata gwiwa zanyi ga kayan suna da kyau." Maman Nana tace Ni dai sarƙoƙin zaki turomin in duba. Suka gama tattaunawa tare da yaba kayan DIJANGALA ENTERPRISE. Hajiya tace "Lafiya na ganku kamar kun haɗa baki ku duka?" Maman Umar Wadda tun fitowar Hajiya ta ke saƙa da warwar kan tunanin ta inda zata fara magana saboda Shatima ya kirata ya sanar da ita komai. Tace Hajiya mun zone a tattauna akan bikin nan. Hajiya ta bita da kallo wanda sai da ta sunkuyar da kai haka ya sa kowacce ta shiga taitayin ta. Duk sukayi tsit saboda irin kallon da Hajiyan ta yi wa babbar su. Hajiya ta soma magana cikin isa. "Sanin kanku ne bana son a yimin ƙarya ko da kuwa yin haka shine zai ceci rayuwata ko? In ba zaku faɗa min abinda ya kawo ku ba kuna iya tashi ku tafi gidajen mazajenku. Na san komai game da abinda kuka tattauna, haka zalika nasan Shamaki ya sanar da ku cewa na sani. To menene abin wani ɓoye ɓoye, bakwamin adalci fa, ban yi muku tarbiyya akan rashin gaskiya ba fa." Duk suka durƙusa a gaban ta suna neman afwarta. Tace "In har maganganun da yazo min da su na al'adar da nake gabatarwa ce to in baku son ranku ya ɓaci ku rufe zancan, sannan ku ɓace min a nan, haka nake ra'ayin tsarin gidana ku bari in na mutu sai ku canza ku yi duk irin yadda ku ke buƙata. 🖊️🖊️🖊️ *HAMSHAƘIYAR UWA🧕🏻* *NA* *HALIMA ABDULLAHI K/ MASHI* _PAID BOOK_ _Kuɗin karatu ₦600_ _Account number 0700549935 Halima Abdullahi Access Bank a turo shaidar biya ta wannan number 08140004302 ko katin Mtn_ _Phone 08140004302_ *DOKA* _Ban amince wani ya ɗora littafin nan a wani Social media ba,ko a maida mini shi Audio ba tare da iznina ba yin haka daidai yake da fuskantar fushin hukuma. A kiyaye_ *Masu son a Tallata masu hajarsu suyi magana ta wannan number 09068032427* *Page 15* Su ka yi ta ba Hajiya haƙuri, ƙarshe dai ta haƙura amma fa ba"a tado da zance ba. Sai dai suka ɓige da tunanin yadda za a gudanar da taron bikin. A'isha ta ce gaskiya ayi Dinner su shirya koma i iyaka su ɗakko amarya kawai, Maman Iman tace haka za'ayi dan ya ɓoye mata ai kuma ranar wanka ba sauran wani ɓoyo cibiya tunda nan gidan za'a kawo ta zai ci gaba da ɓoye mata ne? Maman Umar tace kwarai kuwa domin duk abinda ya ke son ya samu ko ya sani nasan dai zuwa yanzu ya sani. Haka dai suka kira manajan ZEENA Event center suka sanar da shi suna da Dinner ranar asabar in sun karɓi kuɗin wasu to su mayar masu. Suna gama shirya komai Hajiya tana jin su. Suka kira Shamaki suka faɗa masa yace "Duk yadda kuka ce haka za ayi, amma da kun bari sai an kawo ta ɗakin ta sai a yi Dinner ɗin. Maman Umar tace a a ayi Dinner ranar Asabar ,Lahadi a ɗaura aure, Monday taron Hajiya. Yace shike nan sai ku buga mata katin da zata baiwa ƙawayenta da na shiga gurin Dinner ɗin." Ba matsala wannan ta katse wayar bayan ta faɗa masa hakan. Hajiya tace sai ku ɗinka wa amaryar kayan da zata saka a shagalin." Maman Iman tace kubar komai na shirya amarya a hannuna. Suka ce mun bar miki dama kece 'yar gayu. Ta ɗaga waya ta kira DIJANGALA ENTERPRISE ta faɗa mata cewa zata turo mata hotuna wasu lessis cikin 'yan Swizaland ɗinnan ta turo mata su zata saka kudin yanzu. To haka dai suka yini har kusan magriba sanan suka watse. Na tashi da zazzaɓi amma haka na ci gaba da aikin gida domin nasan ciwon na rashi ji daga masoyina ne. Dayake anyl hutun boko hakan islamiyya an bada hutu tunda aka yi saukarmu, dan haka Jamila ma suna gida. Ta same ni kwance ga dumamen tuwao na da kunu na kari a gabana. Tace "Wai don Allah ke haka kike son a kai ki gidan mijin?" Nace Jamila ina ganin Yaya ba wani sona da yake yi, hawaye suka soma zubo min. Ki duba fa Jamila ba zuwa ba kira ko saƙo na kira ya ƙi ɗagawa. Jamila cikin sanyin jiki tace "Nima dai inata yin waswasi amma kawo wayar ki mu gwada wata dabara." Umma ta leƙo tace wai jikin ne kin kuwa sha maganin? Nace Nasha tace harda gajiya ,bari inje gurin Umman Amina inji batun zannuwan gado da labulaye da muka yi magana. Muka ce to. Jamila ta rubuta saƙo kamar haka.. Yaya Aliyu barka da War haka, nice Jamila ƙanwar Baby, bada sanin ta na ɗauki wayar ,na turo saƙon nan ba. Baby bata da lafiya tun cikin dare, ta suma ta farfaɗo amma jikin da sauƙi yanzu, nace ta sanar da kài tace abarka ka faɗa mata. Kana cikin uzrori, amma ta bar saƙon cewa in ajalinta ne ya zo dan Allah ka jagoranci gawarta zuwa kabarinta ,kuma ka yi mata addu'a. Na saki baki lokacin da Jamila ta ke karanta saƙon. Nace ke ina kika samo wannan iya tsara zancen? Tace "Haba Yaya Baby kina mace baki san yadda za ki dagula lissafin namiji ba, in ya dagula miki naki,? Ni nan da kike gani na in har na fara soyayya za a sha fama." Nace duk yadda kike kallon abin ba haka bane. Amma mu jira lokacin sai mugani yanzu dai tura masa wannan saƙon muga ya abin zai zama. Minti kamar biyu da tura saƙo har na soma fargabar ko ya gani ya share, sai ga kira, zan ɗaga Jamila ta amshe wayar tare da faɗin dakata tukunna handsfree. Ta yi sallama,, yace "Baby" Tace Jamila ce Yaya Baby ta samu bacci. Yace "wai me ya faru ne Jamila?" Tace To ni dai tun juya bangane mata ba, ta damu wai baka zo gurin sauka ba, kuma baka ɗaga mata waya, wannan dai shine mafarin ciwo har tana suma, mukam har mun sare amma yanzu da sauƙi, sai dai fa ba cin abinci ga dumamen safe ya nan har kokon bata ci ba. "Innalillahi wa'inna ilaihira'un! To an kaita Asibiti ne?" 'A 'a ko magani taƙi sha sai wasiyya take bari. Yace ina zuwa ya kashe. Muka sa dariya, Jamila ta ce "Yanzu zai zo. Nace in su Umma sukaji fa? Ta ce ke zaki aɗa musu? Barshi ya zo." Umma tana ɗaki ta kwanta. Muka ci gaba da tattaunawa kamar minti ashirin da gama yawa sai ga kira ya kuma shigowa. "Waye? Na tambayi Jamila da sauri ta nuni min fukar wayar kafin ta ɗaga. Tace Yaya. Yace "Kizo gani a waje tace to. Ta kashe wayar. Na miƙe zaraf tace ina zakije? Kwanta kawai ki jira ni. Ta fita wai sai naji kishi Jamila zata gurin masoyina, amma nasani ba wani abu bane. Sai dai duk da haka na ji tsoro na laɓe ina jiyo muryata tana maimaita masa. Yace ya zo ne muje asibiti, tace ai da sauƙi kuma Umma na bacci Abba baya nan kaga ai badama aje amma ka shigo kaga jikin nata. Da gudu na juya na kwanta kan 'yar tsummar katifar mu na rufa. Yau ne karo na farko da Yaya ya shigo cikin gidanmu, duk da gidan talakawa ne ko ina siminti ya ɓurje amma fes a share ko tsinke ba zaka gani ba. Ta je ɗakin Umma ta ɗakko sallaya tazo ta shinfiɗa masa a gefen katifar inda muke salla. Ƙamshin turare sa ya cika ɗakin kamar na tashi zaune, amma ba dama dole umarnin Jamila zan jira a wannan lokacin. Ya ce haka jikin ya yi shine bata sanar da ni ba. Jamila ta ce Wallahi ta hana, yanzu dai bari in tashe ta. Yace "A'a barta kawai Jamila ta taɓa ƙafa ta tare da faɗin Yaya Baby! Na yi miƙa kaɗan dama fuskata na kallon bango na juyo a hankali, sai na sauke idanuna kan angona, na tashi zaune da sauri na zuba mishi ido. Jamila ta sulale ta fita ƙofar ɗaki. Yace Baby ya jiki? Nace na samu sauƙi ya akayi ka sani? "Jamila ta sanar da ni, ki daina damuwa saura kwana nawa mu zama a tare na har abada Baby, kwana biyar kacal." Na lumshe ido na ware su a kan fuskarsa, me yasa baka zo min sauka ba? "Nazo Baby, kun yi karatu ku duka, kin yi ke ɗaya kina kuka suratul Muhammad wanda nima sai da na zubda hawaye, ashema kece shugabar ɗaliba, kin amshi kyautuka harda na ladabi babban baƙon ku wani Basarake ya baƙi kyautar kayan ɗaki yadda ya yi ta jawabi akan ki shine duk kishi ya kama ni, na tafi domin sai naga kamar yana sonki gashi mai hali kar ki juya min baya." Na sauke ajiyar zuciya tare da haɗiye wani ƙududu da ya tokare a zuciya ta. Nace Alhamdulillah ashe ka zo, Yayana warke ciwon da ke damuna a zuciya na matsin na ƙara yin ƙasa da murya, nifa. lokacin bana cikin hayyacina ni dai kunnena ya ji lokacin da yake sanarwar zai min kayan ɗaki, kuma in zaka harbe ni bazan iya faɗa maka kayan da ke jikinsa ba, na san dai akwai baƙin glashi a idonsa. Kuma ko shine ƙaruna a kuɗi ya yi kaɗan bai isa ya raba zuciya ta da sonka ba. Shine ka ƙi ɗaga kirana tun kafin ranar sauka, shin ko me na yi maka? Yace "Abubuwa ne Baby baza ki gane ba, amma ba da wannan wayar na fita ba ranar sai da na dawo na ga kiran amma kiyi haƙuri. Ya kalli robar gefe na, ki tashi ki karya. Ban musa ba na matsa kusa da robar na buɗe, nace Jamila bani cokali. Ya kalli tuwon shinkafa da miyar kuɓewa ɗanya. Ta miƙo ya amsa, nace to kaima kac,i ko baka cin tuwo? Yace "Ni na karya, ke dai ki ci." Na ci kaɗan nace nasan baza ka iya cin abincin gidanmu bane. "Saboda me?" Ya jeho min tambaya. Nace to ka ci, in gani. Ya amshi cokalin sannan yace waya girka?" Nace ni mana. Ya sa cokali ya ci dan ƙarami sannan ya ƙara. Naji daɗi ya ce me kike son cin in aiko maki anjima? Nace babu, yace to zan miki aike zan koma tunda kin samu sauƙi. Ya kira Jamila ya bata dubu ɗaya yace ta siyo min Maltina. Na rakoshi har soro yace in koma kar in fito zai zo ya kawo min kuɗin Party. Jamila ta dawo siyan Maltina tace ƙwaya biyu na siyo kisha ɗaya ni kuma in iragewa su Jafar canjin a baiwa Umma inta tashi. Nace zan rage mata itama ta ɗansha saboda Ummar. Jamila tace ba gashi ya zo ba, amma ke kuka da ƙunci kawai ki ka iya sai kiransa ya na ja miki aji. Nace Jamila ai na daina raina wayonki wannan shiri haka, kinga yadda jikinsa ke rawa har tuwon nan ya ci. To haka dai muka ci gaba da tattaunawa har Umma ta farka. Saura kwana biyar biki mutane sai tsegumi ake yi ba aga ina yin wani gyaran jiki ba. Harda muka yi maganar da Jamila tace ko mu yi wa Umma magana. Nace a a mu barta. Umman Amina dai ta kawomin wasu jiƙe jiƙe ina sha,da wani tsimi. Sai kuma wata kaza nan mara daɗi akace in cinye. Saura kwana huɗu biki kuwa aka kira Abba daga Gandu wai yaje zai ɗauki kayan da akayi masa alƙawari. Da ya kawo kayan sai maƙocin mu aka roƙa gidansa ya tashi ya yi sabo zai gyara ya zuba haya, aka zuba. Banje kallo ba, amma an ce harda dinning table kaya irin na masu kuɗi abin ba a magana. Ranar ya aiko min ta katin ɗaurin aure dana Dinner. Muna ta juya katin Dinner wai a ZEENA Event gurin da gwamnoni da manyan masu kuɗin Kano suke shagali. Jamila tace "Ni fa na soma zargin Yaya nan kamar yana basaja." Nace ke ba wani basaja kinsan yana musu yaron shago, kuma suna mutunci tsaf zasu iya bashi. Jamila ta ce haka ne kuma. Muka samu Zuhra da Amina muka soma rabon kati. Labari ya zaga lungu da saƙo za a fita perty a bikin Baby kuma ZEENA Event center. Nan fa sai surutun wasu suce ɗan karya ne, wasu suce ƙila gadin gurin ya ke har gida waɗanda ba su samu kati ba suke zuwa wai a basu saboda son ƙwaƙƙwafi. Ango bai zo ba sai ranar Alhamis. Ya zo bayan magariba wai yana sauri, yace gobe Juma'a in shirya ni da Jamila Yayarshi zata zo ta kai ni gurin wadda take musu lalle. Yace itace zata miki duk wani gyara, kuma sune suka shirya Party. Nace to yace in faɗi me nake buƙata, nace ba komai dama ai kuɗin perty ɗin zai bada. Ya fito dubu goma yace duk da haka ga wannan kiyi haƙuri ni baza mu haɗu ba sai a gurin Dinner ranar asabar. Nace to za a zo a ɗauke mu ne? Yace e za a kawo motoci ya yi wa abokansa magana insha Allahu. Na ce to na gode. Yace in shiga gida. Na shiga soro na tsaya ya wuce, na dawo na leƙashi ya tafi da sauri, farin ciki ya mamaye zuciya ta. Sai naga su maman Fati suna leƙensa suma dama Fatin ta wuce muna tsaye. Nace kai mutane akwai su da son saka kai cikin damuwar wani. Da na shiga na sanar da Ummar na bata kuɗin, tace to ai sai kuje da Jamila ko? Na ce shima haka ya ce,nace to kuma wa zai taya ki aiki? Tace ba komai ai 'yan Kurna tun yau zasu zo kin haɗa kayan naki kin cire wanda zaki baiwa Jamilan da su Amina? Nace e nawa ai suna cikin bako Jamila ta kai kusa da akwatuna. Tace to in kunje dai ku kama kanku kar a sake ayi wata rashin kunya." Ƙarfe sha ɗaya ya kira ni yace gashi nan ta turo direba yanzu zai yi sallama da ni. Muna aje waya ɗan sako na shigowa muka yi sallama da umma muka fita. 🖊️🖊️🖊️ *HAMSHAƘIYAR UWA🧕🏻* *NA* *HALIMA ABDULLAHI K/ MASHI* _PAID BOOK_ _Kuɗin karatu ₦600_ _Account number 0700549935 Halima Abdullahi Access Bank a turo shaidar biya ta wannan number 08140004302 ko katin Mtn_ _Phone 08140004302_ *DOKA* _Ban amince wani ya ɗora littafin nan a wani Social media ba,ko a maida mini shi Audio ba tare da iznina ba yin haka daidai yake da fuskantar fushin hukuma. A kiyaye_ *Masu son a Tallata masu hajarsu suyi magana ta wannan number 09068032427* *Page 16* Rantsastsiyar mota ce mai numfashi muka shiga. Na dai san mun wuce gidan gwamna daga nan ban kuma gane ko ina muke ba, sai wani damfareren gida na ga mun shige. Muka bi bayansu zuwa wani falon. yace mu zauna tana zuwa ya fita. Wata mai kama da Aliyu ta fito, cikin fara'a ta yi mana sannu da zuwa muka sakko muka durƙusa muka gaisheta. Tace "Ku zauna kan kujera ai ke Antyna ce ta nuna Jamila. Jamila tace gata nan fa. Taɗan zaro ido cikin mamaki tace na zata kece. Jamila tace ni ƙanwarta ce. Na sunkuyar da kai ina mamaki yadda kowa ke ɗauka Jamila ce Yaya ta ko dan ta fini cika ido da 'yar ƙiba. Wata yarinya ta kawo mana kayan marmari da Lemon roba. Ni dai ruwan na sha. Ta kira ni cikin wani ɗaki tace kiyi haƙuri bana raina ki bane ɗauki waccan rigar ki saka ki yafa mayafinta ga shi can. Sai ki fito da takalmin can ki saka in zamu fita. Cikin mamaki nace to. Ta fita na saka doguwar baƙar riga tana ta ƙamshi, na yafa mayafin na riƙo takalman. Jamila ta zaro ido tana faɗin "Kinga yadda ki ka yi kyau kuwa?" Ta fito da makulin mota tace ku muje. A gaba tace na zauna muna tafe tana min 'yan tambayoyi har mukaje wani gida. Ƙamshi tun daga waje. Matar ta amshe mu sai naga ta y i mamaki da tace nice amaryar. Tace wai Maman Iman me yasa baku bata maganin gyara na murmurewar jiki ba? Tace "Nima ban ganta ba sai yau, kuma mun zo a makare, nan zan tafi in barta, ki yi mata komai duk abinda ya kama har ƙunshi dan Allah ki fito mana da ita saboda surutun mutane. Matar tace baki da matsala sai dai kuma su kwana. Tace "To ba damuwa ko Antyna?" Ta kalle ni. Nace bari dai mu kira Ummanki sai ki faɗa mata. Tace to ku kira ta ɗin. Suka yi magana da Umma sannan ta bani wayar Umma tace a kula da kai sosai in kunga wani abu ba daidai ba ko baku gane ba ku min magana a waya." Nace "To" Na kalli Maman Iman na ce ƙanwata za ayi mata ƙunshinne? Tace "A yi mata mana itama duk abinda take so, amma karfa ta kai amaryarmu kyau. Cikin tsokana ta yi maganar mu kasa dariya. Nasha azaba a gyaran jiki amma dana kalli fuskata sai da nace nice kuwa. Aka zuba min ƙunshi ƙamshi kuwa sai tashi yake duk inda na motsa. Jamila ma an mata ƙunshi, sai wasu abubuwa da take bani da madara ina sha. Washe gari ta kuma min hayar jiki. Sha biyu sai ga Maman Iman ta rungume ni tana faɗin amarya ta fito, yanzu sai tafiya gurin wankin kai. Tasha mamaki da ta ga gashin kai na da aka gyara har gadon baya. Tace mu Fulani ne nace a a, amma an ce asalin Kakarmu ta gurin Uba Buzaye ne. Daga can sai shagon kwalliya acan mukayi salla ta kawo mana abinci muka ci, sannan aka soma kwalliya, ban san cewa yamma ta yi ba, sai da Umma ta kira ni wai ina muke ga mutane sun soma cika gida 'yan zuwa party. Na bawa Maman Iman wayar nace kiji wai masu zuwa gun party sun zo sun cika gidanmu. Maman Iman tace bari in faɗawa Ango ya aiko da mota ita amarya daga nan gurin kwalliya zamu wuce. Umma tace shike nan. Ta kira Shamaki ina jin muryar shi yana cewa '"yar uwa wai ina yarinyar nan ne ko muryar ta kin ce bazan ji ba a tausaya min. Tace "Ba za kaji ba sai kun haɗu anjima, ka aika motoci gidan su a kai mutane gurin party yanzu. Yace "To" suka yi sallama. Ta dube tace "Ni na hana angon ki ya kira ki." Azuciyata nace na gode Allah da yasa nima ban kira shi ba. Na sunkuyar da kai ina murmushi. Tace nafi son lokacin da zai ganki sai yaga kin canza gaba ɗaya har muryarki ko bata baki wani haɗi ba ne? Jamila Itama aka mata kwalliya ta kawo mana kaya Jamila ma wani leshin Maman Iman ta bata tace kici albarkacin amarya ko za su yi miki kayan cikin nata ne gashi kin fita ƙiba. Azuciyata nace ko da yaushe tasa akayi min ɗinkin ko gwada ni tela baiyi ba. Kamar ta san na saƙa hakan a zuciya tace da kayan ki da kika cire akayi gwaji. Nace Allah ya saka da alkhairi. Jamila ta saka cif. Suka shirya ni cikin wata doguwar riga bayanta yana jan ƙasa gashi ta ɗame ni da suka gama komai aka kaini gaban madubi. Maman Iman ta kaini ta ce "Kalle ki." Cikin mamaki nace ni ce haka! Suka sa dariya. Nace ko Umma uwar da ta haifeni baza ta gane ni ba. Suka yi ta ɗaukana a hoto. Nan dai muka nufi mota don ana ta matsawa da kira. Ina bayan mota Jamila a gaba Maman Iman ita ke tuƙi. A harabar gurin motoci na alfarma iya .ganin mutum ta ce da Jamila ta fita ta duba mutanan unguwarmu ko sun samu shiga. In taga waɗan da ba su da pass ta yi mata magana zata sa abarsu su shiga. Ta dube ni "Amarya ki zauna bari naje mu fara shirya shigarku. Na kuma tsakiyar kujerun bayan tafiyar su ina sake kallon kaina a madubi gaskiya ni kyakkyawar ce a she ko dai don an canza min kamanni ne. Naji a ƙwanƙwasa gilashi Jamila ce ta buɗe tace kinga kuwa 'yan unguwa maza da mata a wajen gate wasu. ma ni dai ina ganinsu ko magana bata taɓa haɗa mu da su ba. Nace kije ki faɗawa Anty Maman Iman in sun shigo arziki ne. Tana tafiya Yaya na zuwa ya ci wata shadda kalar sararin samaniya, ya yi mugun kyau a zuciya ta nace ashe dai akwai mijin Nobel da gaske. Ya shigo ya zauna kallona ya ke ya kasa magana. Nayi ɗan murmushi, Yaya ka yi kyau sosai. Yace "Baby baki lura na kasa magana ba, gaskiya ne ina son gayu sosai zaki na gyara min jikin ki haka ko?" Na ɗaga kai alamun e. Ya ciro waya ɗan matso muyi hoto. Gabana ya fadi Allah ya sa ba taɓani zai yi ba. Na ayyana a zuciyata. Hularsa da ɗankwalina ne kawai suka haɗu ina jin sautin numfashin sa. Na lumshe ido domin wani yanayi na samu kai na. Cikin murya ƙasa ƙasa yace "Buɗe ido Amaryata ki kalli camara. Na kalleni a cikin wayar munyi mugun kyau. Ƙwankwasa motar ya tsaida ɗaukar hotunan da ya ke yi. Abokansa ne da su Anty. Maman Iman tace "Wai waya ce kazo ne? " Yace Na ga shigowar ki fa, nasan amaryata ta na wurin ki. Nan dai muka fito aka nufi shiga Hall. Yaransu ne aka jera a gaba sun sha wata farar riga bulawus su kuma mazan sun sha shadda mai kalar ƙasa. Sai su Antys da Jamila da Zuhra da Amina suma dai an sako su saboda Maman Iman tace ina ƙawaye na tace gasu nan. Leshi dai suka sa daidai ƙarfinsu amma fa kowacce da kalar nata. Sai abokan Yaya ni yau nataɓa ganinsu. Hawaye naji yana bin kumatuna lokacin da na kalli gurin da jama ar dake gurin a domin ni, a zuciya ta faɗi na ke, Allah na gode maka. Allah ka sa in masa biyayya. Da muka zauna yace kalle ni sai yaga hawaye. take ya rikice ya sunkuyo gurin kunne na yace. "Baby me akayi ba daidai ba? Kukan me ki ke yi ne amaryata." Na motsa baki zanyi magana sai muryata ta soma rawa, yace "To karki yi maganar, ya kai hannu ya ciri hankici a aljihunsa fari tas yasa hannu ya dafa ɗankwali na ta baya yana tsane hawayen fuskata cikin lallashi yana faɗin haba soyayyata zaki ɓata gayunki mana." Na ware idanu ina kallon fuskar shi a zuciya ta ina godiya ga Allah daya min baiwar miji irin wannan. Ya ɗakko ZEENA table water ya tsiyaya a kofi ya bani. Yana faɗin "Sha masoyiya." Sanyinsa ya ratsa maƙogwarona dai dai lokacin da MC yace " Kai Don Allah ku tafawa Ango da Amarya haƙiƙa zai iya kula da amaryar nan tasa da kyau. Sai mukaji tafi da sowa sam na manta akwai mutane a gurin duk zatona mu biyu ne sai sautin dake tashi, na manta da akwai dubunan jama'a da ke gurin. To haka dai aka ci gaba da shagali, abinda ya ɗaure min kai kalaman da MC ke faɗa in zai ambaci ango ko danginsa, sai ya ce Shamaki Aliyu Ali Baita shugaban rukunin kamfanonin ZEENA. Ɗaya cikin Antys ɗin shi ta zo gurinmu sai ya ce Hajiya A'isha Ali Baita kenan uwar marayu da marasa ƙarfi shugabar ZEENA Foundation. Tofa! kaina ya soma kullewa duk yadda aka yi akwai abinda Yaya ya ɓoye min. Haka da aka zo matakin rawa, sunyi watsi da sabbin 'yan dubu dubu har abin tsoro ya bani. Kuma ga masu kirari suna ta yi wa Yaya Shamaki Ali Baita. Suna faɗin shaharar ɗan kasuwar nan mai kuɗi da ake labari ko kwatance dashi. To haka dai aka kawo wani cake mai mugun girma inda muka yanka ni da Yaya, abin dai zallar al ajabi. Da aka tashi suka shigar dani wani ɗaki aka kawo min abinci, nace na ƙoshi ni dai buƙata ta in je gida inga Ummana tun jiya ban ganta ba. Sukace ai daga goben zaki jima baki ganta ba. Daƙyar dai na ci ɗan cake na sha ɗan lemo. Yaya ya zo yace in zo ya maida ni gida Abbanmu ya kira shi yanzu. Haka dai muka firfito kowa ya kama hanya. A baya na zauna shima haka abokinsa kuwa ne ke kanmu. Ya zura min ido ni kuma na ƙi kallon sa, hardai na kasa jurewa na sa hanuwana na rufe fuskata ina dariya. Yace "Baby ji nake kamar in wuce da ke gidana gobe in an ɗaura shike nan." Na saci kallon sa, dama ana yin hakan? Abokinsa da ke jan motar ya sako baki da faɗin "Za a fara yau." Na dafe bakina cikin kunya. Yaya yace Alhaji Shamsu me ya kawo kunnen ka. Shima ya sa dariya tare da faɗin "Ba da ku nake ba Ango da Amarya." Yaya ya matso daf da ni, ya kwantar da kan shi a bayan kujera yadda har ina jin iskar numfashinsa, a gurin kumatuna, ya ce, "Baby in ɗan taɓa hannunki ƙunshin nan ya min kyau sosai. Na waiwaya na masa wani irin kallo, ya hure ida nuna, na lumshe su gaba na yana wata irin faɗuwa. A cikin kunne na naji kalmar ina son ki Babyna. Na naɗe hannuwa na a ƙirji, domin tsigar jikina naji ta yi wani yarr tamkar zazzaɓi zai rufe ni. Alhaji Shamsu yace zumuɗi. Duk muka sa dariya. Haka muka iso bakin lungun mu. 🖊️🖊️🖊️ *HAMSHAƘIYAR UWA🧕🏻* *NA* *HALIMA ABDULLAHI K/ MASHI* _PAID BOOK_ _Kuɗin karatu ₦600_ _Account number 0700549935 Halima Abdullahi Access Bank a turo shaidar biya ta wannan number 08140004302 ko katin Mtn_ _Phone 08140004302_ *DOKA* _Ban amince wani ya ɗora littafin nan a wani Social media ba,ko a maida mini shi Audio ba tare da iznina ba yin haka daidai yake da fuskantar fushin hukuma. A kiyaye_ *Masu son a Tallata masu hajarsu suyi magana ta wannan number 09068032427* *Page 17* Yace tsaya nan direba mai sa ido. Muka fito shine ya riƙe min rigata ta baya na tsallaka kwata, muka isa ƙofar gidanmu yace shiga ciki zan kira ki anjima. Na shige cike da ɗokin ganin Ummana. Gidan ya cika da Jama a, 'yan ƙauye da na birni. Innarmu ƙanwar Ummanmu ta rugo da gudu ta rungume ni tana cewa ga amarya. Na samu su Umma da su Umman Amina a ɗaki suna ta tattaunawa. Umman Amina ta ce ke 'yan nan dama ɗan gida Ali baita ne mijin naki. Na yi sukuti ina ta sauraron su, suna ta murna. Ni kuma zuciyata bata murna, kuma na kasa gane me yakamata inji farin ciki ko takaicin Aliyu ya min ƙarya. Ina son insan gaskiyar abinda ake faɗi. Na canza kayan jikina Umma tace inje gidan Umman Amina can zamu kwana da su Jamila domin gidan ya cika. Nace to sai inyi salla acan. Umman Amina tace zata aiko mana da tuwo in an kaɗa miya. Nace ina su Amina tace in yi gaba sunje ɗakko markaɗen kunun safe ita da Jamila da Zuhra. Naje Dakalin ƙofar gidanmu na zauna jiran su domin dai abikin nan sune ƙawaye. Sai ga Fati mai Awara, tace "Jamila ina amarsu." Nace ba Jamila bace. Ta zauna "Ashe kece da kanki, haba gaskiya naji ƙamshi duk ya buɗe ko ina, amarya mai maganar zuma, kaga matan manya. Ai munje perty ke kuwa ina kika zaƙulo ɗan gidan Alhaji Baita? mamakin da kowa ke yi kenan Baby." Nace ina ya zaƙulo ni dai, wannan amsar kuma shine zai bada ita ɗan gidan Ali Baitan. Tayi dariya tare da faɗin "Koma dai menene kin dangwalo, yanzu ina zaki." Nace gidan Umman Amina can zamu kwana. Tace "Bari in faɗawa Umman mu sai inzo mu kwana ai duk mune ƙawayen Maimuna ma tun ɗazu ta ke zuwa nemanki." Cikin mamaki nace to sai kunzo. Na bita da kallo ina mamaki wai harda Maimuna yarinyar da ko magana bata min saboda Babanta yafi Kowane uba sukuni a lokonmu. Muryar Jamila ta sa na waiwayo ina kallon su sun taho da bokitai a kansu na markaɗe Jamila tana ta ba su labarin gidan Maman Iman da kuma guraren data kaimu, wai ita tun daga nan ta san dangi arziƙi ne. Nace to Zubaina ku nake jira ku shiga ku aje ku zo muje. Suka fara murna ga amarya ga amarya. Da sauri suka fito. Zuhra ta ce, "Wannan ƙamshi Yaya Baby har kin koma kalar bota ɗin." Nace kun fiye surutu. Muka kama hanya Jamila ta ce "Su Mariyan can lungun dama ƙawayanki ne?" Nace wai ta gidan gurasa? Tace "Su." Nace ina ni ina waɗannan marasa kamun kai? Tace "To sau uku suna zuwa nemanki, kuma na gansu gun party sunsha rawa." Na kwashe da dariya, nace yanzu Fati mai awara ta barnan, wai zasu zo mu kwana kin san su dawa? Tace 'a' a, su da Maimunar gidan Alhaji. Gaba ɗaya muka sa dariya. Zuhra tace "Ki kore su ne, saboda abokan ango suke yin wannan shishshigin ko suma wani zai ce yana so." Amina ta ce "Haka ne Yaya Baby. Na ce ba kora su zo. Kuma ba lallai akan tunanin su cewa Yaya shi ɗan Ali Baita ne tunda har zuwa yanzu banji daga bakinsa ba. Jamila tace "Haba yaya Baby karmu ruɗa kan ki mana, wace sauran hujja ki ke jira? Jiya ganin shi da 'yan uwansa ya isa hujja, ƙila ya dai ɓoye miki ne ko yana son ya miki bazata ne, kuma salon ya birge, Abba cewa ya yi shi tun a katin gayyata ya so ya fahimci haka." Da sauri nace wake da katin a cikin ku? To ni ban ma tsaya na kula da katin ba. Amina tace "Mu shiga gida in ɗauko miki." Tabarma muka baza a tsakar gida muna zama sai ga su Fati, nan suma suka saje da mu ana labari. Nace Amina ina katin? Tace "Shi nake dubawa na Abbanmu ne Allah ya sa bai fita da shi ba." Can kuwa sai gashi ta samo. Na kunna fitilar wayata ina karantawa. Tabbas iyalan marigayi A Baita. Shi kuma a sunansa sai aka sa Aliyu A.Baita, sam ban gane komai ba sai yanzu. Na miƙa mata kati tare da faɗin biri ya yi kama da mutum. Na Dulmiya cikin tunani, nifa zuciyata da son Aliyu Shamaki mai tsare kaya ko sai da kaya shagon mai gidansa a Zeena plaza kanti kwari ta kamu. Bawai Aliyu Ali Baita ba. Na ɗauki wayata na soma rubuta saƙo zuwa ga Yaya. Kalmar da na soma rubutawa itace...Yaya akwai babbar matsa. Ina buƙatar sanin wasu abubuwa game da kai. Ina tura saƙon na tashi naje nayi alwala na shiga ɗakin Umman Amina nayi salla, ina idarwa Jamila tana shigo wa, ta zauna kusa da ni. "Yaya baby wai lafiya naga duk kin canza tunda ki ka karanta katin nan?" Na ce Jamila in har ta tabbata Yaya shine ɗan Ali Baita to bazan aure shi ba. Ta rufe min baki da tafin hannunta. "Menene haka ki ke faɗa, maimakon ki yi murna ki ce Alhamdulillah Allah ya miki gata sai kuma ki ɗebo wata rigima? Na ce Jamila masu kuɗin nan suna da wulaƙanci, in zargin nan ya tabbata Hajiyar da muka je gurinta ita ce mahaifiyar sa. Ta yaya zan iya zama da wannan Hamshaƙiyar. Me yasa har zuwa yau bai faɗa min gaskiyar shi ba, dubi yadda 'yan matannan suka cika gidan nan saboda kawai zan auri ɗan Ali Baita, ki tuna yadda za su yi dariya a lokacin da ya sako ni. Gara yanzu aji ni nace na fasa. Jamila tace "Duk wannan hasashen ki ne, waya faɗa miki zai sake ki?" Nace ya saki mata uku ni ce 'yar gwal? Tace "Shawara ta ɗaya ki kira shi ku yi magana." Nace na tura masa saƙo. Ta amshi wayata da sauri ta shiga ta karanta abinda na rubuta. Ta kalle ni. "Wayyo Allah Yaya Baby, ya zaki masa irin wannan saƙon." Nace To me zance masa. Sautin kiran wayata ya katse mu, ta miƙo min "Gashi yana kira." Na ɗaga tare da sallama. Yace "Babyna kin ci abincin kuwa?" Nace ba zan iya cin abinci a halin da nake ciki ba. Yace "Subhanallah me yafaru?" Nace baka ga saƙon na ba kenan? Yace Gaskiya babu wani saƙo da ya shigo cikin wayata. Ki faɗa min menene?" Amma kafin nan ƙifara cin abinci. Nace ba'a gama miya ba tukunna. Yace "To ki jira ni." Ya kashe wayar. Na kalli Jamila, na san ya gani kawai zai ce min bai gani bane. Jamila ta ce "Ki bari ya zo ɗin karki yanke hukuncin da ba haka bane." Shigowar 'yan gidan gurasa ya sa raina ƙara ɓaci. Jamila tana ta lallashina da ƙoƙarin nuna min cewa ƙila ya ɓoye min ne saboda wani dalili nashi. Ta tilasta min zuwa gurin da 'yan matan suke muka gaggaisa ana ta hirar gurin Party tare da kallon hotunanmu. Duk kowacce tambaya take wai ina muka haɗu da shi. Nace shi ya kawo kanshi har lungunmu, inda ya ganni. Maimuna tace gashi daga gani yana mugun sonki, ko ina a hoton yana kallonki. Wayata dake hannun Jamila tana tura min hotunanmu a wayar Mariya ta soma ringin. Jamila tace ga ango yana kira, na amsa duk suka bi ni da ido, na ɗaga da sallama. Yace ina ƙofar gida. Nace sai ka ƙaro gaba gida na ƙarshe a lungun can zamu kwana. Yace "To ki fito ki tare ni." Nace to. yace "Kada ki kashe wayar fa." Nace to. Na saka takalmi ina ce musu bari in dawo, sai naji kusan duk sun amsa da to amarya. Ina fita yana ƙarasowa ya aje ledar hannunsa, ya zauna a bakin dakalin. Na ƙarasa na zauna, na gaida shi cikin girmamawa kamar yadda na saba. Ya amsa sanan yace "Faɗa min wane saƙo kika Turi min?" Na sunkuyar da kai cewa na yi akwai matsala. Na ɗago na dube shi, Yaya ka faɗa min waye kai?" Yace "Me kike son sani?" Kai ɗan Ali Baita ne? Na jeho masa tambaya. "Me yasa kika tambaye ni?" Na juya masa baya, ka bani amsa kawai In shine me zai faru?" Ya sake jeho min tambaya. Ban yi soyayya da ɗan Alhaji Baita ba, da Aliyu na yi soyayya talaka mai tsaron kantin Zeena plaza. 🖊️🖊️🖊️ *HAMSHAƘIYAR UWA🧕🏻* *NA* *HALIMA ABDULLAHI K/ MASHI* _PAID BOOK_ _Kuɗin karatu ₦600_ _Account number 0700549935 Halima Abdullahi Access Bank a turo shaidar biya ta wannan number 08140004302 ko katin Mtn_ _Phone 08140004302_ *DOKA* _Ban amince wani ya ɗora littafin nan a wani Social media ba,ko a maida mini shi Audio ba tare da iznina ba yin haka daidai yake da fuskantar fushin hukuma. A kiyaye_ *Masu son a Tallata masu hajarsu suyi magana ta wannan number 09068032427* *Page 18* Kuma shi zan aura inyi rayuwa da shi cikin yanayin akwai ko babu. "Ya matso daf da ni. Yanzu ma dashi zaki rayu Baby ni yaron Alhaji Baita ne amma ba ɗan daya haifaba, ɗan jire kanti ne." Na juya muna fuskantar juna.ka tabbata? Yace "Na tabbata kuma zan tabbatar miki da zarar an gama bikin nan." Na sauke ajiyar zuciya tare da faɗin to duk kashe kuɗin nan da ake yi fa? Kuma a katin gayyata ka ɗora sunan Ali Baita. Ya ƙara ƙasa da murya. "Ba zan iya hana su kyautata min ba Baby, saboda mun zama ɗaya da su mutanen kirki ne hatta katin su suka buga sai ganin shi na yi. Kuma don Allah kar ki damu kanki kar ki saurari kowa abinda na faɗa miki kawai zakiji, ko mutane sun yi wata magana duk hasashe ne. abinda ni na faɗa miki shine kawai zaki y arda da shi kinji ko?" Na sunkuyar da kai nace To. Ya sauke ajiyar zuciya, "Yawwa amaryata, amma fa kin ɗaga min hankali da ace ni ɗan cikin Baita ne yanzu shike nan gobe sai a fasa aurenmu?" Na turo baki tare da faɗin e mana, haƙura zanyi. Ya yi ' yar dariya maimakon kiyi murna kin samu mai kuɗi." Nace taɓ aini bana ra'ayin auren mai kuɗi gara ma in muna tare kayi kuɗin, ance suna da wulaƙanci ga sakin mace ayi ta mata gori, arziki, kaga kaina ka rabu da matanka har kashi uku kaga kuwa dole in yi ta kaina. Haka iyayen ta ba a basu daraja dan suna talakawa. To da in aure ka ka sake ni Yaya gara ba muyi auren ba. Ya ɗan yi shiru. Can yace "Baby da aure da saki iri daya ne da mutuwa, nasan kina damuwa ne saboda na saki mata har uku, kar ki damu da wannan ke dai ki yi aure bautar Allah ,kuma Baby ni da ke alkawarin da zan miki duk juyi bazan sake ki ba, kema ina son ki yi min alƙawarin cewa duk wahala bazaki guje ni ba." Cikin sauri nace na yi maka. Yace to "Mun kashe wannan wutar gobe kamar haka kina gidana jiya Abba ya kira ni zancan kafi na kayan ɗakin ki. To jiyan ana fenti ne yau kuma mun tashi da perty , amma gobe bayan ɗaurin aure sai akai kayan ko?" Nayi murmushi Wannan maganar ku ce ta manya. Yace "Haka ne, to ga kaji nan a leda da madara da sauransu don Allah ki ci ki ƙoshi kinji?" Nace kai ka ci abinci? Yace "Hajiya a baki yau ta bani fura wai tun jiya banci komai ba kamar wani ɗan ƙaramin yaro ta ajiye Ni ta bani." Muka sa dariya. Nace kai ɗan gatan Hajiya ne. Yace "Ke 'yar gatana ce, zauna in baƙi a bakin kema." Nace'A'a. Yace "To shike nan ki koma ciki ki ci sosai don Allah Alhaji Shamsu ya kawo ni yana jirana dan ya koma gurin iyalinsa da wuri." Nace wai dama kana da Abokai? Yace "E mana duk zaki san su a hankali." Na ɗauki ledar na shiga ciki, shi kuma ya wace, na dawo ina leƙenshi ya tafi da sauri. Yanzu kam hankalina ya kwanta koda ƙarya ya yi min." Jamila ta tare ni da faɗin "Me muka samu ne?" Nace Yaya da abinsa wai yasan banci abinci ba shine ya kawo min naman kaza. Nan fa suka ɗauki sowa da guɗa suna faɗin wannan ango yana ji da ke. Kaji uku ne nace Jamila ta cire ɗaya ta ɗauki madarar ta haɗa ta kai wa su Umma, na ɗauki nawa nace Amina ta raba musu. Muna gamawa sai ga mutane sun shigo da guɗa wai za ayi kamu, suka fesa min turare irin dai yadda ake yi a al'ada aka gama kowa ya watse sai mu 'yan kwana. Cikin dare bacci ya ƙaurace min wai gobe zan zama matar aure, na ɗakko waya ta ina kallon hotunanmu da Shamaki, faɗin cewa na dace ma ƙauyanci ne, Allah ne kawai ya bani shi ba wayona ko wata dabarata ba a kyan fuska duk da yana namiji ya fi kuma ko da ina mace ban san a gaba ba, amma ni da kaina na san bani da wata ƙira mai ɗaukar hankalin maza ɗan gara ko daga sama. Wata zuciyar ta ce gobe kamar yanzu muna tare da shi. Gabana ya fadi ni ba ƙanƙanuwar yarinya bace na san meye aure duk da bansan shi a zahirance ba, dole inji fargaba ban sani ba ko ina da budurcin da ya tambaye ni ko babu. Sai dai ina da tabbacin ban taɓa zina ba. Ni dai har kiran sallar farko idona biyu ina ta saƙe saƙe daga binasi bacci ya ɗauke ni. Da safe na yi wanka cikin shadda Maman Iman ta kirani ta ce ta turo direba zai kaini gidan kwalliya. Na sanar da Umma tace to muje da Jamila amma karmu jima kafin ɗaura aure mu dawo. Yau ɗin ma dai kamar jiya, tsara min kwalliya tamkar wata 'yar tsana. Ta bani wasu kayan tace inyi canji cikin wani ƙaramin akwati sai wata leda mai ɗauke da sarƙoƙi a jikin ledar an rubuta DIJANGALA ENTERPRISE. Kenan acan suka sai min. Ta sa direba ya ɗakko mu. Layin mu cike da mutane da motoci ya tsaya nesa kaɗan da lungunmu dan ba gurin fakin, muka sauka mukayi masa godiya muka nufi lungunmu. Jamila ta ce "Yaya Baby kalli ƙofar gidan Abbansu Zuhra ki ga motoci kuwa.?" Nace kinsan ɗan kasuwa in yana da mu'amala da mutane za su zo masa. Tace "kin dai ƙi yarda." Nace wai bana faɗa miki yadda muka yi da shi ba a jiya, amma kina ta musu, ki barsu in an kaini sun ga gidansa sai su samuwa kan su lafiya. Mutane sai kallona suke masu min Allah ya sanya alkhairi suna yi har muka shiga gida. Ya cika ɗajim da mutane sai kallo ya dawo kaina. Ƙawayen dolena suka shigo duk sun sha wanka, sai ga mai hoto da me ɗaukar bidiyo aka shiga ɗaukar hotuna. Can Jamila ta miƙo min wayata "Kina da saƙo daga ango." Na duba da sauri, "Alhamdulillah! Alhamdulillah!! Alhamdulillah!!! Na zama mijinki Baby." Na ɗago a sanyaye na kalli Jamila, idanuna suka cika da hawaye, ta ce "menene"? Sallamar Abba ce ta sa na maida kallona gareshi, yana faɗin "Alhamdulillahi an ɗaura Allah ya basu zaman haƙuri. Sai hawayen suka kwaranyo bazan iya fassara ko kukan menene ba. Jamila ta ce "Kingani zaki ɓata kwaliyarki ke da ki ke ta zumuɗin zaki auri Yaya meye na kuka?" Nan abokan wasa suka taso ni a gaba. Jamila ta dubi Abba zai fita ga mai hoto ana ta ɗauka. Tace Abba don Allah zo a mana hoto." Sai akace a kira Umma. A nan kam ban jure ba sai da na zubar da hawaye sosai hoton har su Jafar da Baba Habu ƙaramin mu ga cikin Ummanmu. Jamila ta jani ɗakin Umma na canza kaya ta ɗan goge min inda hawaye ya min jirwaye a fuska. Muna fitowa sai tankani ake yi dan kyau. Atamfa ce mai adon zaiba, ta ɗauki ɗinki. Lokacin aka ce ga angwaye za su shigo su yi gaisuwa a yi hotuna. Nan naga munafircin mata. kowacce ta maido hankalinta ƙofar shigowa. Yaya da Abokansa ƙamshin su ne ya fara shigowa kafin su shigo, ya yi kyau cikin shadda mai ruwan siminti tsananin kyan shaddar shine ya bayyana tsadar ta. Ya murza hula saƙar Gabas wadda ta tafi da kayan. Yadda kowa ke kallon sa haka nima nake ƙare masa kallo, fara'a fuskarsa ita ta bayyana tsantsan farin cikin da yake ciki.Haƙorin Makkansa yana haskawa, ina son haƙorin sosai ya ƙara masa kyau. Suka tsugunna suka gaida su Umma abokan wasanmu sai tsokanar sa suke yi. Jamila ta kamo hannuna tana faɗin "Kifito kin laɓe kuma kina leƙensa." Na fito ya bini da kallo. Abokan suka ce mai hoto ya matso. Haka dai aka yi ta ɗaukar hotuna Ango fara'a ta kasa yankewa. Murya ƙasa ƙasa yace "Baby ina son mu yi magana ga shi ko ina mutane." Nace to ya za ayi? Ko zamuje gidan Usman Amina tunda duk suna nan? Yace " Ina ne?" Nace inda ka same mu jiya. Ya ce "To." Har abokan muka taka da Jamila soron gidan muka shiga muka bar abokan da Jamila a waje tana yi musu tayin abinci suka ce walima zasu tafi yanzu. Muna shiga Yaya caraf ya kama hannuwana cikin ɗoki, duka biyun yana musu wani irrin kallo, tsigar jikina ta tashi yarr, zan kwace sai yace "Kiyi haƙuri Baby an ɗaura mana aure, tun a ,jiya ina son in shafa wannan fulawar amma bani da damar aikata haka, saboda nasan shara'a bata bani dama ba." Na jure yana shafawa da lallausan hannunsa sai kurum naji ya sunbaci bayan hannuna, ya kafe ni da ido, duk tsoro ya bayyana a fuskata cikin rawar murya nace, Yaya kar fa wani ya ganmu. Ya girgiza kai, muryar shi a sarƙe ya ce in ɗan rungume ki Babu?" Na kwace hannuwana da sauri, sannan nace suna jiran ka a waje fa. Ya matso naja baya da sauri nace Jamila. Ta shigo tana faɗin "Menene?" Ta kalleshi har lokacin ni yake kallo, batare da ya lalle ta ba ya yi mata alama da hannu wai taje. Ta yi yar dariya ta fita. Ya matso ina ja baya har naje bango daf dani ya tsaya ya saki ɗan murmushi. "In Jamila ta iya cetonki yanzu anjima ko gobe wa zaki kira?" Gabana ya yi mummunar faɗuwa, na ganni wata 'yar tsuntsuwa a gabanshi. Muryata na rawa nace ina son inje in sha ruwa ne Ya yi murmushi. Yasa yatsa ya lakuci janbakin leɓena, ya lasa akan harshen sa. Sannan ya kauce gefe tare da faɗin "To soyayyata, kunga ga hanya nan nasan dai yanzu sai. in an rako ni, ko da yake zamu yi waya aiko?" Da sauri na nufi ƙofa ina cewa e zamuyi waya. Sai na ji ya saki dariya tare da faɗin "Matsoraciya." Mukayi sallama da su suka tafi ina ta bin Yaya da kallo, ashe dai shima ɗin ba kyalle bane. Sannan ya ƙara jefa ni cikin tunani. 🖊️🖊️🖊 ️Maganganun shi sun jefa ni a fargaba, na shiga ɗimuwa sosai, harma na kasa cin komai, kuka na yini yi, mutane suna zaton kukan barin gida ne, duk da cewa akwai hakan amma dai fargaban karon battar da zamu yi da Yaya ya fi komai ɗaga min hankali. Da taimakon su Jamila na yi ta canjin kayana. 'Yan kafin kayan ɗaki sun dawo duk sun ruɗe suna bada labarin gidana Gidan Hajiya Zeena ne. Sun gigice da ciye ciye da aka basu, wasu kuma suna murna sunga Hajiya Zeena. Nace to kenan dai Yaya ƙara rufe ni ya yi. Jamila ta ce na faɗa miki, to ke menene na ki na ɗaga hankali mai maimakon murana Allah ya baki sai ki yi masa godiya. Shiru na yi domin bazata fahimce ni ba. Da yamma motocin ɗaukar amarya suka iso motoci na gani a faɗa. Na ƙanƙame Umma ina kuka sai lokacin naji duk auren ya fita kaina. Tace "Meye hakan kuma, ki tafi Allah ya bada sa'a ya albarkaci zaman ku ina fata zaki ɗauki dukan shawarwarin da muka baki. Haka Umman su Zuhra ta ɓanɓare ni ina kallon Umma tana hawaye muka Fita gidan su Abban su Zuhra shida Annan mu suka min nasiha suna ta maimaita min in yi haƙuri, in zama mai yawan haƙuri har sai da na fara tunanin kalmar nan da ake ta nanata min akwai dalili. Muka fita nabi layinmu da kallo ta zuciyata ta sake karyewa sai naji tamkar na tafi kenan. Ta ciki mayafi ina ganin harabar gidan na gane, kai tsaye suka shiga da ni falon Hajiya cike da mutane tana hakimce a kujerarta kamar yadda na zata, tana ta yi mana sannu da zuwa. Aka kaini gabanta aka zaunar, aka ce ga 'yar ki Hajiya mun kawo miki. Tace "To Allah ya yi musu albarka ya sa mun ƙulla alkwairi ina fatan kun faɗa mata yadda zata zauna da mijinta lafiya. Yanzu ku kaita ɗakinta, nawa shi'anin sai gobe inda ita amarya zata girka mana abinci tare da taimakon masu aiki ta bamu ni da mutane na, ina fatan zaku zo domin ku ci girkin 'yar tawa. Sai kallon kallo ake yi. Umman Amina tace insha Allahu. Ta ce Maman Umar ta jagorance mu zuwa ɗakina. Aljannar duniya, haka kowa ke faɗi, ni dai ina lulluɓe a zaune bakin gado ina jin yadda suke labarin kayan kyale kyale da na kallo kyan ɗakin ɗaki sun tafi da mutanen don haka sai waɗan da suka yi kafin abin ya zame masu sabo. Haka dai ina zaune bakin gado kai na a rufe kowa sai bani shawara yake yi ki kwantar da hankalin ki ki yi biyayya ki ci arziƙi iyayenki su ci. Da haka duk aka watse, nace don Allah a barnin su Jamila sa dawo zuwa dare. Aka bar su bayan kowa ya watse sai na cire mayafi daga fuskata na fito falo ina ƙarewa ɗakin kallo. Na ruɗe wai ni Rabi 'yar magini ni ce da wannan dakin. Kenan zanyi murna da ƙaryar yar da Aliyu ya min? Na tambayi kai na. Abinda ya ƙara ɗaukar hankalina shin me ya kawo hoton babban baƙonmu na gurin sauka inda yake bani allona? Naje na zurawa hoton ido, a take na gane komai, wannan babban baƙon wato dai Yaya ne, duk cikin raina min hankalin da ya yi ne. Jamila ta zo gurin ta tsaya a gaban hoton ta sa hannu ta dafa ni, tace "Wannan shigar tamkar babban baƙon gurin saukar ku." Nace shine, tace "Ashe babban baƙon ɗan uwan su ne?" Nace shi kanshi ne a hoton nan kenan kinga shine babban baƙon. Jamila ta yi dariyar mamaki ta lakuci kumatuna tare da faɗin "Lalle shi wannan ɗan wasan kwaikwayo ne, to bin ya birge sosai." Ta zaro ido, kamar ta tuna wani abu. "Kenan shine ya sai kayan ɗakin nan?" Na sa mata hannu a baki na toshe domin bana son su Zuhra su ji. A hankali nace tabbas shine. Muka zubawa juna ido nace ina tunanin yadda zan yi masa zancan. Jamila tace. "Kawai ki shere azuwan baki gane ba." Nace barshi yadda ya yi wasa da hankalina haka zan yi da nashi, sai ya faɗa min da kansa cewa shine. Jamila tace "Duk ba wannan ba, ya zakiyi da girkin gobe?" .... Nace ko a jikina ban wani damu sosai ba, nafi damuwa da yaudarar da Yaya yamin, ni gaskiya a tsarina bana son in auri mai kuɗi saboda gudun wulaƙanci, na yi ƙasa da murya me mata uku suka yi masa duk ya raba su da 'yayansu ya kore su? Bakya tunanin yadda zan zama bazawara? Bakya tuna yadda masu min dariyar nuna min farin cikin na dace zasu koma yi min dariya tare da Allah ya ƙara?Dan haka wannan yafi zancan yin girki a gobe. Abinna na iya shi zanyi, kuma sun san daga ina aka ɗakko ni. Jamila tace "Allah ya dafa miki, kuma zan zo goben in taya ki." Nace kefa nan zaki kwana kuma ba zaki shiga kicin ba. Ta zaro ido. "Rabani da faɗan su Umma, na dai dawo goben kamar yadda suka ce za a iya zuwa amma gaskiya bazan kwana ba. Na yi alamun kuka, tace "Garama kar ki sa a ranki. Haka dai Su Fati da sauran 'yan layinmu suka buɗe kofar suka shigo da sallama duk zatona sun tafi. Jamila tace "Na zata kun wuce?" Sai sukace sai an rako ango tukunna. Bayan sallar Isha aka kawo abinci tuwon shinkafa da miyar alayyaho ta ɗau kifi da nama, sai jalaf ɗin shinkafa ta ji naman kaji ga lemuka masu sanyi. Nan suka hau ci. Ni kam duk da ina jin yunwa amma zan iya cin komai ba, saboda far gaba sai dai ruwa na ɗauka na sha. Bayan sun gama Jamila ta ce su Amina su kai kayan ita kuma za ta gyara gurin, sai tsiya suke min wai ba su ga laifina ba in banci ba anjima da kazata ta amarci anjima kar in cika ciki yanzu. Ni dai ban kula su ba, sai fargaba da suka daɗa jefani ciki. Takwas da rabi ina gyara fuskata bayan nayi salla, sai kiran wayata ya shigo. Cikin faɗuwa gaba na sa wayar a kunne ban iya ko sallama ba. Yace "Baby" a sanyaye nace na'am. Yace "Gamu nan shigowa yanzu ke da su waye?" Gaban ya sake faduwa naji kamar cikina ya karta. Nace su Jamila ne. Yace "Ok sai ki gyara sosai ki rufe jikinki nake nufi." Nace to. Yana aje waya Maman Iman tana ƙwankwasa ƙofa suka buɗe mata suka gaisheta kai tsaye ta shigo cikin ɗakin ɗayar mai min kwalliya ce. Tace Karamar mu babbar mu ga ango nan zuwa bari a gyara min ke. Na gaishe su cikin kunya da girmamawa. Sannan nace shima yanzu ya kira wai zasu shigo. Tace Bari in ƙara in dakatar da su. Ta dube ni, ya naga duk jikin ki ya yi sanyi? Na yi ɗan murmushi nace ba komai. Tace "Ni dai sai kinyi kyau." Ta kirashi ta dakatar da su. Nan fa ta kuma gyare min fuska da kwalliya, aka turare min gashi da jiki, ta ɗakko lafaya tana cewa "Cire a layyace min ke cikin wanna lafayar." Mai kwalliya tace ina kika sai wanana lafayar? Tace kayan 'yan gayu ne DEEJANGALA ENTERPRISE kin san kayan su akwai kyau ga sauƙi, kuma abin birgewar kin ga wannan lafayar ta jikin ta, zai wahala ki ganta jikin wata. Mai kwalliya tace don Allah zaki bani number ta. Maman Iman tace zan baki mana. Ni dai ina jin su na ta labarinsu, na ɗau kyau kamar 'yar tsana. Maman Iman tace "Ki rufe min fuskar ki kar abokai su gane Kinji ko? Kya dai gaishe su ta cikin mayafin." Nace to. Sukayi sallama wayar ta tayi ringin, sai ta ɗaga tana cewa, "Ku shigo ango mun. kammala" Su Jamila suka .shigo suna buɗa fuskata suna leƙawa suna faɗin kyau da ƙamshi. Ni dai shiru na yi domin fargaba da wani irin tsoro suke gigita ni. Cikin haka aka ƙwanƙwasa ƙofa suka amsa sannan Fati ta tafi ta buɗe Sai kurum naji ina faɗin Hasbunallahu wa ni'imal wakil. Suka zauna falo ina jiyo muryar Yaya yace "Jamila kiranta." Ta shigo ta ce Yaya Baby ki fito. Na ce na shiga uku Jamila wallahi tsoro nike ji. Hannu ta riƙe min ta yi min jagora muka fita domin na ƙi buɗe ido. Tace "Menene abin tsoro, na bita muka fita, sai naji ta zaunar da ni a kujerar kusa da shi, ya kasance har ina jin ƙamshin turare sa. Shi kuma ya kashe ni da ido duk da fuskata a rufe a mayafi amma ina kallonsa. ...... Abokansa sun yi addu'o'insu sannan suka yi nasiha sannan suka haɗa da tsokana aje min kuɗi suka yi, sannan kuma suka ba ƙawaye suma wai na sayen baki, duk da basu ga fuskar amarya ba. Yaya yace "Alhaji Shamsu ku maida yaran nan don Allah." Alhaji Shamsu yace su fito mu kai su. Da sauri na riƙe hannu Jamila jikina yana rawa nace ke k i tsaya sai gobe. Tace "Yaya Baby so ki ke yi Abba ya kusan halaka ni, da duka kenan.' Yaya ce koma ki zauna kinji ai gobe zaku dawo ko Jamila? Na saka kuka yace "Jamila ki tsaya to sai ki kwana." Ya yi maganar cikin lallashi. Tace Wallahi ta sani in har na kwana Abba zai min dukan tsiya, ita tana nan lif a ɗakinta. Yace "To Kiyi haƙuri kibarta ta tafi. Nace to ka kira Abba ɗin ka faɗa masa. Ya ɗakko wayar ya kira amma tana kashe. Na sakar mata hannu jikina a sanyaye, na yi baya na zauna akan kujera. Suka tafi ya raka su bakin ƙofa suna wucewa maida ƙofa ya rufe. Yasa hannu ya buɗe fuska. Tabarakallah Masha Allah. Ya furta cikin jin daɗi, ya saka yatsa ya ɗauke siraran hawayen fuskata ya tsugunna a gabana. "Haba Baby ai kin gama hawaye insha Allahu menene zai saki tashin hankali haka? Faɗa min damuwar ki yanzu?" Cikin rawar murya nace gida zan koma. Ya zauna "Me zaki yi acan?" Ya tambaye ni a gigice. Nace ba komai ni dai ina jin tsoro ne. Cikin mamaki yace "Tsoro kuma? To tsoron wa?" Na yi shiru. Ya ce "Ko dai kin ɓoye min ne dama baki so na?" Nan ma naƙi magana. Ya miƙe cikin damuwa. Ni kuma na ci gaba da ɗan kukana. Yace "Kinga bana son wannan kukan tashi in kai ki gida." Nace Abba zai dake ni ne. Sai naga ya yi 'yar dariya, yace "In har bazaki je ba to gaskiya ki yi shiru ki faɗa min abinda ki ke tsoro kuma ki faɗa min gaskiya in dama ba so na ki ke yi ba." Na rasa abin cewa sai dabara ta faɗo min, ai dama ya yaudara ni, nace Ka ɓoye min gaskiyar ka, kuma ni bani da ra'ayin auren mai kuɗi ina tsoron wulaƙanci bana son in zama bazawara ne. Sai naga ya yi dariya, sannan ya miƙe. "Zo muje. Ya kawo hannu zai kama nawa, cikin firgici naɗan ja baya, ya kalle ni har sai da naji wani iri. Yace "Muje" nabi bayan shi dai dai lokacin da Juma ta nufo sashen mu tace masa "Ga kaji amarcin inji Hajiya tace a kawo Uban ɗakina." Yace Je ki kai tana nan ko ta shiga ciki? Tace "Tana nan Azima tana mata tausar ƙafa Yace "Ta ƙafa. Haka kuwa mun samu Azima ta na yi mata tausar. Ya rusuna cikin girmamawa, nima na yi kamar yadda ya yi. Yace Hajiya an samu wata ' yar damuwa ne. Ta kalli Azima "Je ki kwanta." Azima ta kllemu sannan ta fice. Hajiya ta zuba mana ido "Damuwa kamar ta me?" Ya ce game da yarinyar nan ne wai sai na kaita gida yanzu, tun da ta gane cewa ni ɗan Ali Baita ne ban faɗa mata ko ni wanene ba, ya kwashe duk yadda mukayi tun kafin a ɗaura aure da nace talaka nan nake so ya faɗa mata. Hajiya tana gama ji tsaf, sannan tace "Ke yaya sunan naki ma?" Yace Rabi'a. Tace ɗago kanki ki dube ni. Na kuma sunkuyar da kai, ta ci gaba da faɗin "Ni ce mahaifiyar sa Aliyu Ali Baita. Ni ce Hajiya Zeena wadda dai ki ke ji, shine autana a cikin 'yay'anmu biyar da muka haifa da Ubansu Alhaji Ali Baita, ya gaji mahaifinsa a suna, ya gaji mahaifinsa a kuɗi ina nufin dukiya, ya gaji mahaifinsa a biyayya, ya gaji mahaifinsa a soyayya. shima bai taɓa neman wani abu na rasa ba, abu ɗaya ya kasa samu shine mace ta gari ko ince miki soyayyar gaskiya shine dalilin ɓoye miki asalinsa da ya yi kuma da ran yin hakan kwalliya ta biya masa kuɗin sabulu." Ta numfasa sannan ta ci gaba. "Kar kiyi alaye kice wai ke bakya son mai kuɗi, wannan labari ne domin mai kuɗi shine abin so, dalilin haka ne ya ɓoye miki cewa shi mai kuɗi ne domin ya samu soyayya ta gaskiya wanda muke sa ran cewa ya samu, bai kamata ki shigo da wata damuwa kuma a irin wannan daren na f arko mai albarka da tarihi a gurin duk wata ɗiya mace, ba." ta nuna ni da yarda ke bari in faɗa miki wani abu wanda ban taɓa faɗawa surukai na ba face 'ya'yan da na haifa. Ta ƙara rage sautin muryarta sannan ta nuna . Shatima tashi ka tafi, zan sa Juma ta r ako ta. Ya miƙe tare da faɗin sai da safe Hajiya , tace "Kana jina, karka damu kuma kabi komai a hankali kar ka manta da addu'a acikin ko a wane irin yanayi ka ksance." Ya ɗan shafa kai tare da faɗin i nsha Allahu Hajiya. Yana bada baya tace, "Ban yarda cewa bakya son ɗana ba, domin ya cika ta ko ina ɗa namiji. Zanfi yarda in kince kina jin tsoron daren farko, tabbas 'yarnan daren nan na fargaba ne ga duk wata mace wadda ta alkinta mutuncita ko akasin haka, wadda bata san namiji ba, tana tsorata ya zata kasance, a farkon al"amarin, haka kuma wadda ta san namiji a waje tana tsoron kar fa angon ya gane." "Rabi'atu" Na ɗago na dube ta. Sannan na sake sunkuyar da kai. Taci gaba da tambaya ta. "Kin kasa cin binci yini yau? " Cikin raunanniyar murya nace Wallahi ni ko yunwar ma bana ji. Tace da zaku fito gida me kikaji a zuciyar ki ? Na sunkuyar da kai.Tace "kar ki damu faɗa min ni mace ce, 'uwa kuma kaka. sannan ina son in tantance in har da gaske baki son ɗana bazan bari ya ɗora miki idda ba zan sa ya sahale miki yanzu kuma ya kai ki gidan iyayen ki. Sannan ki sani ba a min karya a gidan nan ki amsa min tambayoyi na gaskiya." Nace Ni ada ina son sa sosai amma yau gaba ɗaya ji nayi aure ya fita a raina, ko da muka zo gidan nan zuwa yanzu sai naji na daina son shi,Ni tsoron sa ma nake ji gaba ɗaya. don Allah Hajiya ki ce ya maida ni gida. Ta saki murmushin mai sauti, ki nutsu kar ki ruɗa kanki, kin zo wani mataki mai mahimmanci a rayuwa wato daren farko. Ta matso ta kama hannu na tace, "Yata bana manta irin wannan daren saboda kima da martabarsa, na ina faɗawa 'yayana martabar wannan daren domin na taɓa kasancewa a cikinsa, da a ce ni marubuciya ce zan rubuta in wallafa babban kundi mai shafi sama da dubu ina mai bayyana kima da darajar wannan daren. Don haka ina mai baki shawara kar ki bari vwannan daren ya tafi a haka batare da kin zama Hamshaƙiya a gurin mijinki ba, zama Hamshaƙiya a gurin miji shine ya ke sa ki zama Hamshaƙiya a idon duniya har zuwa kan ahalinki. Ƙila yanzu duk bazaki fahimci abinda nake son sanar da ke ba, sai nan gaba. Da mata za su san darajar su game da wannan daren da sun kasance suna ririta kansu tamkar dai ƙwai a kan kanfa, baza su yi guje guje ba, bare wani hawa keke ko bishiyoyin kamar yadda likitoci suka faɗa. To har bare su biye wa wani azzalumin namiji ya rusa musu rayuwarsu y a goge sumu wannan tarihin da za su kafa na daren farko kafawa ta har abada. .... Ta kama hannun ta riƙe shi a cikin na ta tace "Abinda kawai nake so da ke shine ki cire tsoro kina son mijinki na tabbata da haka, sannan ki zama mai juriya a duk yanayin da yazo miki a wannan dare, sannan duk da cewa baƙon al'amari ne zai riske ki, ina son ki bashi haɗin kai da goyon baya hakan zai rage miki shan wahalar da ki ke jin tsoro, sannan kar ki manta da addu'a baki sani ba ko da Allah zai baki rabo a yau. Ina fatan kin gane karatun da ba kowace uwa ke iya zaunar da 'yar ta ta koyar da ita shi ba wannan karatun ina karantar da iya 'ya'yana ne amma yau na karantar da surukan kuma ina fata kin gane." A hankali nace na gane. Tace "Yawwa akwai wani abin kuma ina zuwa" Ta kira Juma ta zo da sauri tace gani. Hajiya ta ce, 'Kije ki dafa min madarar shanun nan da aka kawo ɗazu kofi ɗaya ki zuba zuma ki kawo mata yanzu." Juma ta ce to, ta juya da sauri . Ni kam ina cike da mamakin wannan al'amari bansan yadda zan fassara Hajiya ba, kuma ban iya gane domin ni yi don ta taimake ni ko kuwa domin jin daɗi da nutsuwar ɗanta, koma don me ta yi dai na yaba mata har ga Allah, kuma ta ƙara girma da kima a ido na,ta sanar da ni wani ilmi wanda hankulan mutane ba sa kaiwa gurin. Sannan na lura gidan ba'a magana mai ƙarfi sam sai kuma sai kaga duk suna ji. Shamaki kusan so uku in ya zo zance da nayi magana zai ce in ke yin ƙasa da murya ba a nesa yake ba. Hajiya ta katse min tunanin da cewa "Kina yin al'ada ne?" Na girgiza kai alamu 'a 'a, ta ce "Yawwa in kin in komai da zai faru tsakanin ɗa mijinki ya faru to kuma kar ki zama raki da ƙazanta, ki tashi ki gyara jikinki kar ki kwana cikin ƙazanta na san dai tunda da karatunki ba sai an koya muku wankan janaba ba, niyya ce kawa ta raba su da wanda ki ke yi a duk wata. Na sunkuyar da kai sannan kaɗa kai alamun haka ne. Juma ta kawo madarar Hajiya ta amsa ta miƙamin tare da faɗin maza shanye yanzun nan zata riƙe miki ciki kuma zata taimaka miki sosai gurin saukar ni'ima haka zai rage muku raɗaɗi ke da shi." Na kurɓa na ɓata rai. Tace "Maza shanye, ki ɗauke numfashin in bakya ra'ayinsa kar ta tada miki zuciya." Haka na shanye duka na aje kofin, tace "Yawwa Allah ya bada sa'a. Juma zo ki kai ta Allah yi muku albarka dukan ku. Hannuna Juma ta kama muka nufi ɗakina tace 'yarnan kin shigo da ƙafar dama, alamu suna nuna cewa Hajiya ta yarda da ke ke kuma sai kiyi ƙoƙarin cin waɗansu jarabawa da zata miki na tsawon shekara ɗaya in kin tsallake kin zama matar gida, in kin kasa sai ki bi sauran matan mijinki ki koma gidanku koda kuwa kin haihu ki dire abinda ki ka haifa. Gabana ya faɗi na maimaita kalmar Jarabawa a zuciyata. Ta dafa i lokacin da muka iso ƙofar ɗaki na, naga har kin tsorata, zan baki satar amsar jarabawa guda ɗaya, ki zama mai gaskiya da faɗin gaskiya duk rintsi ko da kin aikata ba dai-dai ba, ya kasance ya kasance kin faɗi gaskiya. Tace To. Zantukan Hajiya da na Juma sun yi matuƙar tasiri a zuciyata har ma naji na rage fargaba sannan na samu ƙwarin gwiwar miƙa wuya. Sai dai kuma zancan Juma ya zo min da sabon firgici. Ta sa hannu ta ƙwankwasa tare da sallama. Ya bata izni ta murɗa ta buɗe sannan ta koma baya alamun in shiga. Yana zaune a kan kujera yana kallon TV ya ke yi, ya canza kayan shi zuwa baƙar Jallabiya mai surfani ruwa zaiba, ya yi kyau sosai. Na nufi kusa da shi na zauna, bazan iya fassara yanayinsa ba, amma nafi zaton ya ji haushi ne. Nace Yaya, ya dube ni "Na '"am Baby in zo muje ne in kai ki gidan?" Na sunkuyar da kai ina wasa da gefen lafaya ta, ka yi haƙuri bazan ƙara ba. Ya ɗora ɗan yatsan sa a. kan leɓunana, ki daina bani haƙuri. Ya kama hannuna "Tashi muje ki kici abinci zaki ci ko?" Na ɗaga kai alamun e. Na ɗaukar wa kaina alwashin bazan masa gardama ba. Ya kama hannuwa na biyu ya damƙe cikin nasa. Yace "Baby Wato shiyasa duk Duniya in aka cire Allah da ma'aiki sai Hajiya bana iya kai kuka na ga kowa, ba wani aboki ko wani ɗan uwa, ni ban taɓa zuwa mata da matsalata bata share min hawaye ba duk abinda ya ta so min ya shige min duhu gabanta nike kai shi kuma sai ki ga komai ya zo min cikin sauƙi. Ina son ki riƙe ta a matsayi mahaifiya kuma kar ki ɓoye mata damuwar ki ko a kai na ne, sannan duk rintsi .kar ki koyi ƙarya komai nauyi gaskiya to ki faɗa mata koda laifi ki ka yi Ina son ki Baby ina son mu zauna na har abada." Na ce Insha Allahu zan yi duk yadda ka ke so. Yace "Amma yanzu dai kina sona ko?" Na ɗaga kai, ya miƙe tare da faɗin Muje muci abincin. Anjere komai kan wata shimfiɗa ta fata ga abubuwan tada kafaɗa a gefe, tsakiya an rubuta Amira sai aka yi hoton zuciya sai aka rubuta Shamaki. Ya buɗe flas ɗin kaji tare da faɗin "Al 'adar gidanmu tana shan banban da ta wasu ina fatan zaki jure, maimakon ki ga abokaina sun kawo kazar amarci da gasashiyar kaza sai ki ga Hajiya ta ta aiko ko?" Nace Ni bansan ma yaya ake yi ba. Ya yanko tsoka da wuƙa ya ce "Buɗe baki." Na sunkuyar da kai sannan na ɗago na karɓa. Haka dai mukaci kaɗan muka tashi, ya kama hannu na zuwa cikin ɗakin baccina ya soma warware min lafayar da ke naɗe a jikina tare da faɗin "Ki cire ta ki sha iska ko?" Ya jefata kan gado na hankalin sa ya ɗauku zuwa gashin kaina, ya nutsa yatsun sa a ciki, ya ja zuwa ƙarshe gashi, na lumshe idanu ina jin wani yanayi mai cike da biyu, shuƙi da fargaba. Yace "Wai dama gashin nan da na gani jiya a gurin party na mu ne ba ciko aka yi ba?" Kai na iya ɗagawa domin bana iya fassara yanayin yadda ya kamata. Ya ce "Alhamdulillah kin boye shi a hijabi naji daɗin haka sosai yau na ganshi abin ya birge ni Baby ina son gashi da yawa. Banyi magana ba. Ya sake ni "Ki cire wannan rigar ki yi shirin bacci sai ki same ni a ɗakina." Bansan ɗakin ba. Na faɗa cikin yanayin tausayi. Ya shafi kumatuna ki nemo ɗakin mijinki." Na bishi da kallo ya fice. Naje gaban madubi na tsaya bayan na cire rigar jikina na maida doguwa ta bacci. A madubina ina iya kallon jikina domin rigar babu abinda ta ɓoye. Gaskiya bani da wani shef na irin na mata, ɗan ƙuguna dai gashi nan haɗe da baya, haka ma ƙirjin kamar mai ƙirgan dangi, cikina kuwa sun haɗe da baya, sai naji ina fargaba r karma ya kalli surata ya yi daya sanin aurena. A haka na zura hijabi na ɗauki wayata na kulle ɗakina na fita neman ɗakin mijina kamar yadda ya ce. Na gane ɗaya. ƙofar zata maida ka falon Hajiya, ɗaya kuma ta fita zuwa barandar gefena kai tsaye, sai kuma ga wasu biyu. Na tura ɗayar sai naga ta buɗe, na leƙa wani ƙaton falone na alfarma shigen na Hajiya. Na shiga sai naga ƙofa biyu .na buɗe ɗayar sai naga wani dogon corridor ne, na bishi sai na hangi ƙofofi gudan biyu. Kafin ƙofar sai naga Window na tsaya jikin window na buɗe labulayen a hankali ɗaki ne ƙato mai ɗauke da gadajen yara guda biyar. Kowanne da fitowar sa ta saka kaya babba. A kwance yaran Shamaki ne suna bacci cikin kwanciyar hankali can gefe ga mai kula da su a nata gadon. Na yi musu addu'a kamar yadda Abbanmu ke mana in ya zo duba mu mun kwanta bacci, na tofa musu daga inda nike sai na juya. Tsaye ƙyam yana kallo na. Na ɗan daburce kamar mara gaskiya, nace ban iya gano ɗakin ba, Allah ya sa hakan ba wata al 'adar na saɓa ba. Ya kama hannu na, "Amma kin gano na yaranki ko?" Ya ƙara so ya ɗaga labulen ya kallesu, tun da ki ka zo kin haɗu da su?" Nace 'a'a. Yace "Na faɗa musu cewa Momyn su tana zuwa, san nan wancan gadajen guda biyu na ƙannen su ne, zaki haifa musu ko?" Na rufe fuska. Ya kama hannuna, "Muje ko za'dace tun a daren yau. Ɗakin sa ba tarkace gadone gashi nan kamar suffar ƙwai kalar ruwan zaiba madubi manne a bango sai kuma tafkekiyar durowa ta shafe bango, can ga durowar takalma gata huluna kamar kasuwa, sai gefen gadon sa ga fitilar karatu da Alkur'ani a gefe, sai wani littafi Nobel. Na ɗago na lalle shi. "Ɗakin ya yi miki ko kina son a canza wani abu?" Cikin jin kunya na sunkuyar da kai ashe yana kallona ina ƙarewa ɗakin kallo. "Kiyo alwala mu yi godiya da addu'ar samu zuri'a ta gari." Banɗakin ya birge ni, na zuba wa fuskata ido a ƙasan zuciya ta kuwa farga ne." Bayan mun idar yace "To Bismillah ki zo ki kwanta dan nasan kin gaji zan ɗan matsa miki jikinki sai ki samu bacci ko? Gana ya faɗi. Amma sai kalaman Hajiya suka dawo kunne na, ki zama mai juriya kuma ki bashi haɗin kai hakan zai sa komai ya zo miki da sauƙi." Na miƙe na je gabansa ya kama ni ya zaunar a cinyar sa. Da ace zan iya bada labarin abinda ya faru a lokacin da duk wata mace budurwa zata so ƙwarai ta kame mutuncin ta da kimarta har sai ta riski irin wannan ranar. Cikin bacci naji ana shafa gashin kaina, na buɗe ido a hankali muna haɗa ido, na maida su da sauri na lumshe, komai ke zuwa min tar abinda ya faru, gaskiya namiji mace ce raunisa, domin na tuna yadda mutumin nan ya yi a jiya. Sai Muryar sa a cikin kunne na, ki tashi ni na tafi masallaci. A hankali nace to sai ka dawo. Sai da naji fitarsa sannan na tashi a gajiye na shiga banɗaki. Har na idar da salla abubuwan da suka wakana tsakaninmu kawai nake gani. Na ɗaga bargo zan kwanta sai naga wasu guraren da suka ɗan ɓaci sai dai a canza. Na yi ɗan murmushi, sannan na sauke ajiyar zuciya, tun jiya nake cike da alfahari. Naji shi shiru sai na fita zuwa ɗakina, na watsa wanka na saka doguwar riga baƙa na yafa mayafinta, sannan na nufi gaida Hajiya. Ban ganta a kan kujerar ta ba,sai naji magana ƙasa ƙasa a gefe, ina kallon gurin sai naga ashe sune tana kan sallaya yana gefe ya sunkuyar da kai, kamar mai ɗaukar darasu. Nima naje nayi irin sunkuyon sa a gefenta na fara gaida ita ta amsa tare da faɗin "Ya baƙunta?" Nace Alhamdulillahi. Na ɗan shafi kallon inda ya ke, shima ni yake kallo. Nace Yaya ina kwana.Ya amsa tare da tambayar baƙunta. Hajiya tace tun a waccan ranar na faɗa miki cewa ki daina kiran sa da Yaya, kin san dalili? Na girgiza kai. Tace "Ba ku da wata alaƙa mai kama da hakan ta jini ko ta danga rere, don haka ki ce masa Aliyu, ko ki faɗa masa Shamaki, ko kuma ki faɗa masa suna irin naku na 'yan zamani, amma bana son inji Yaya ɗinnan." Nace to insha Allahu na dai na, dama sunan nasa ne bazan iya faɗa ba. "Jiya kin faɗa duka biyu." Na dube shi da sauri, muka haɗa ido na sunkuyar da kai, sannan na miƙe Hajiya zanje ciki. Tace "To Allah ya shi albarka, kamar ƙarfe goma sai ki fito ku yi mana abincin jama 'a ta." Nace To. .... Na koma na rusuna kusa da Hajiya nace a ƙalla kamar abincin mutum nawa za ayi? Ta zuba min ido. "Me yasa ki ka tambaya?" Gabana ya faɗin Allah dai ya sa yin hakan ba laifi bane. Nace dama dai na tambaya ne domin kar a yi shi ya yi kaɗan ko kuma ya yi yawan da zai zama kamar almunbazaranci, ta kaɗa kai alamun ta gamsu, "Kamar na mutum hamsin za a yi zuwa Saba'in. " Nace To. Ɗaki na koma dan in jira shi ya zo mu karya. Juma ta shigo da babban tire, jere da flas na shayi da na abinci, ga samiru. Na yi mata sannu ta amsa, tace "Ki karya kummalon ki amarya ki maida hankali ga naman da ke ciki waccan Samirar kece mace ta farko da Hajiya ta sa ayi wa irin wannan dahuwar a cikin wancan takardar mai kyalli ga gashasshen nama nan, duk matan da Alhaji Shamaki ya aura ke ce kaɗai bata buƙaci in je in ciro mata zanin gadon da ku ka kwana a kai ba. Saboda haka ina baki shawara ki yi ƙoƙarin cinye jarabawa." Nace Na gode, amma don Allah zan iya tambaya? Kai ta ɗaga. Nace wace irin jarabawace ki ke ta min magana tun jiya? Juma ta yi ƙasa da murya tace "Jarabawar zaman gidan nan ce kuma shekara ɗaya ce, zan sake tambaya ta ɗaga min hannu tare da faɗin ki bi a sannu." Nace To me rashin aiko ki cire zanin gado ya ke nufi? Tace "Kenan ta gane ke kin kawo budurcin bata buƙatar ta ga shaida." A zuciya ta nace Hajiya dai ta matsa wa kanta a wannan fannin duk da na gamsu da bayanin ta. Na sauke ajiyar zuciya, nace, Da ku zamu yi aiki anjima? Ta ce "E dama zan tambaye ki ko mu rage aikin tun yanzu?" Nace Hajiya baza ta yi faɗa ba? Tace "A'a ai ita ba ruwan ta kece zaki kula da komai." Nace to kamar me zaku rage. Tace tafashen kaji in za a soya ne sai ki bamu umarni, da naman rago kuma akwai kifi ma. Nace to ku soya ɗin. Tace "Za ayi pepe ne ko kuwa?" Duk da ban iya ba sai na ce e har pepe ɗin ma kuyi, shima kifin ku yi zan shigo kamar goma. Tace "To aike 'yarnan baki da girman kai amma sauran ko kallo bamu ishe su ba, sai dai ace wanke min wannan yanka min waccan sai sun gama Hajiya ta kasa ci. In kuma har Hajiya bata ci ba to kin faɗi jarabawar farko, daga ranar kun ƙulla. Basa tuna mune gidan mu muka san kanshi. Na yi ɗan murmushi na gode Baba Juma. Da sauri tace "Allah ya yi miki albarka 'yarnan kin san darajar tsofaffi." Tana fita nace Yawwa kai Allah na gode maka da ka bani mafita, sannan wannan kam akwai ta da magana, zanji abubuwa da dama a gurin ta cikin hikima. Naci nama gasashe da yaji na sha shayi da wainar ƙwai, ƙosai da kunun gyaɗa kuwa ko kallon su ban yi ba domin ba baƙi na bane. Amma na damu kasancewar bamu karya tare da ango na ba, har tara saura bai shigo ba, na ɗan kashin giɗa a gefen gado na kira wayar Umma, kamar in shiga ta wayar in ganta, idanuna suka kawo ruwa lokacin da ta ɗauka, nace Umma ina kwana? Ta amsa muka gaisa, na tambaye ta Abba tace ya fita. Nace zan kira shi,ta ce su Jamila za su zo anjima ko ina son wani abu?".Na ce tazo da su Jafar da Baba Habu. Umma tace "To dama suna ta mitar basu je ba." Nace to. Na kira Abba na gaida shi, yana ta min nasiha, hawaye na bin kumatuna. Muna yin sallama Shamaki ya na shigowa, ya tsaya yana kallo na. "Ke da wa kike waya naga kina kuka?" Na miƙa mishi ya amsa ya ce A"bba ki ka kira." Ya zauna yana share min hawaye, "To menene abin kukan kuma?" Ya sakar min cakulkuli, na saki dariya tare da faɗawa kan gado. Yace da fatan kin karya dai ko?" Cikin zolayar nace najira ka baka dawo ba, sai nace ƙila acan ka ke ƙari. Ga mamaki na sai naji yace kamar kin sani, bana iya karyawa da kowa sai da Hajiya, abinda zai baki mamaki ko ƙasar na bari to na bar karin safe har sai na dawo." Na ɓoye mamakina sannan nace abin birgewa ina son irin soyayyar nan tsakanin ɗa da mahaifi. Sai naga ya saki baki ya zuba min ido gaba ya faɗi nace na faɗi ba dai-dai ba ko? sai ya sa hannu ya kuma janyo ni zuwa jikinsa yana faɗin Allah na gode Allah yarinyar nan liɗifi kamin da ka bani ita. Nace kamar ya ke nan fa? Yace A kan karin kummalon da nake yi tare da Hajiya a cikin matana akwai wadda tace wai in auri uwar tawa, dukkan su kamar irin wannan ranar ba wadda bata min ƙorafi ba. wannan mummunar kalma tafi komai ɓata min rai har kuka na yi." Nace bata kyauta ba. Yace ke kaɗai ce baki min ƙorafi ba kuma ban gani ko a fuskarki ba, don Allah kar ki canza kinji?" Na kwantar da kai ƙirjinsa kar ka canza min kaima. Yace insha Allahu. Yace "Bari inje in shirya zan fita kasuwa." Na dube shi ba hutu? Yace matane zasu cika gidan." Nace haka ne, to abinci fa? Ya kama kumatuna, "Za a kai min har kasuwa yau zanci jagwalgwalon Baby Allah ya sa Hajiya ta ci ina roƙon ki ki ƙure basirar ki, abinda baki gane ba ki tambayi Juma." Nace to kuma zan baka mamaki.Ya miƙe zai tafi, nace Yay sai na rufe baki na. Ya saki dariya bari Hajiya ta jiki garama kin yi saurin samo min suna ko kice Shamaki. Na matse kafaɗa bazan iya cewa ba. ."Amma jiya ki ka ce Shamaki Aliyu dan girman Allah! Na nufi gurin shi da gudu na ɓoye fuska ta a cikin shi ina faɗin don Allah ka dai na ɗazu wai har a gaban Hajiya kuma wai zaka faɗa? Muje in taya ka ka shirya ka tafi. Yana dariya yana faɗin "Ok kina korata neko? Muka nufi ɗakinsa, naga an cire zanin gadon an yi shinfiɗa an gyara komai. Nace waya gyara ɗakin nan? Yace "Menene" na yi shiru, yace "Bakya son a gyara ne?" Na ɗaga kai alamun e. Yace"Bazaki iya gyaran ɗakin nan ba." Saboda me? Na tambaye shi tare da zuba mai ido. "Ɓangaren nan yana da girma za a kawo miki mai aikin da zata kula da naki sasan da kuma wasu buƙatunki." Nace kar a kawo min, sannan kuma abar min gyaran nan gefen na ka a hannunna domin Umma da Abba sun faɗa min aikina ne in kula da kai da duk wani abu naka da ka aje a gidanka. Sun ce aljanna ta a nan zan nema amma kai kuma kana son ka hanani samun wannan damar. Na ƙarasa maganar cikin tura baki a yanayin shgwaɓa. Ya aje rigar da ya cire zai shiga banɗaki, ya kama hannuwana guda biyu. "Zanyi ta addu'a ga su Umma ina gode musu da irin ginin da suka min ta tarbiyyar da suka miki, ni suka taimakawa da yarana da zaki haifa min ƙilama har da waɗanda ba ke ki ka haifa ba. Allah ya sa jiyan nan mun samu Zeena." Na rufe fuska ina faɗin shiga wanka kafin ka canza maganar kuma ni ce zan fito maka da kayan da zaka sa. yace "Ni da kayan duk naki ne yadda kika dama haka kowa zai sha, ina nufin duk yadda ki ka shirya ni haka kowa zai lalle ni." Na buɗe durowarsa na tsaya kallon kaya, kaya iya kaya, na yi ta buɗe ƙofofin ina kallon ko wane ɓangare, ɓarin agoguna ne da gilasai na ido, abin dai ya cika ni da mamaki. Na fidda masa wata shadda mai kalar sararin samaniya da malun-malun na je duniya hulunansa na fidda wadda zata dace, har agogo da gilas na cire komai. Yana shafa mai ina kallo yadda suma ta kwanta a sassan ƙirji sa, zuwa ƙwaurin sa, abin ya matuƙar birgeni ni. Ya kalle ni ta cikan madubi, "Zaki taimaka min a bayana?" Na miƙe tare da faɗin sani kawai zaka yi Ni nawa aikatawa ne, na lakuci mai ina shafa masa a baya, ya lumshe ido Baby tsigar jikina tana ta shi, nace in bari ne? Ya ce "A 'a kimin sosai." Ya juyo ya rungume ni, "Baby komai na ki ya yi min." Na yi murmushi. Mu Haka ya saka kayan na wanke shi da turare, na ɗaukar masa jakarsa mai ɗauke da laptop. Na kai shi har bakin ƙofar da zai shiga falon Hajiya. Yace "Yaya Baby a iya nan?" Nace Nice Yaya kuma? Hajiya zata ga cewa daga zuwana har na rako ka zai zama kamar na zaƙe ne. Ya lakuci hancina tare da faɗin soyayyata mai wayo. .... Da na dawo zan shige zan shige gurina sai naji kukan yara, sai na samu kaina da nufar gurin su. Rahin ta yi musu wanka tana ta fama da su zata sa musu kaya amma Mubina bata son kayan da aka ciro musu, ita leshi za a sa mata, Anisa kuma ba wannan takalmin take wa kuka ba, sai an canza. Meema tana kicin kicin saka nata kayan. na shiga nace me ya same su? Cikin girmamawa Rahin ta ce Rigima suke jin yi Anty kinga ga kaya wai kowccen su bata so." Na ce to ki barsu kowa ta ɗauki wanda ta ke so mana ina ganin ai kamar ba matsala ko? Rahin ta ja baya tace "To ku zaɓa amma don Allah kar ku zubo kayan domin shirya su ba ƙaramin aiki bane durowa uku, aiki ne." Nace kije kusa sai su nuna miki sai ki ciro wa kowaccen su yadda ba zai ɓaci ba ko? Ta ce "To " Yara suka bini da kallo sannan suka kasa nuna wanda suke so. Nace In zaɓo muku? A tare suka ɗaga kai. Na dubi Rahin anko ake yi musu kullum?. Tace "Wani lokacin suna sa daban daban." Nace Hajiya tafi son su sa kaya iri ɗaya? Tace "Ban taɓa jin Hajiya ta yi magana akan haka ba ." Na kama hannun su suka nuna min duk abinda suke so, nace to muje ɗakina sai in shirya ku a can. Da sauri suka yarda suka bini Rahin ta bini da kallo. nace ki gyara musu kayan kawai. A Kan gadona nace su hau Meema tace "Hajiya ta hanamu tace gadonmu kawai zamu hau amma banda na manya." A raina nace tofa! Sai nace ai Hajiya bata nan kuma ni bazan faɗa mata ba. Sai suka kalli juna, Mubina ta zau a kan kafe ɗin gaban gado, Meema ta ce "Hajiya ta faɗa mana in bata nan Allahnta yana nan, kuma zai ganar da ita inhar muka yi ba daidai ba. Na sauka kan Kafet ɗin batare da na sake magana ba, nace bari a fara shirya Anisa ita ce 'yar ƙarama ko? Meema ta ɗaga kai, sannan tace "Anty ke ɗin wacce ke ma nan gidan ki ke?" Nace ni Mominku ce, ba sunana Anty ba. Mubina da Anisa duk suka kalle ni , Mubina tace "Kema a nan gidan ki ke?" Nace e mana ga ɗakina ma. "Kece Momin da Dady yace zaki zo in anyi biki?" Inji Meema. Nace la! ashe ya faɗa muku, to ni ce. Anisa tace "To Momy anyi bikine?" Nace anyi jiya yau ma za ayi. Suka fara murna." Na gama shirya su muna ta 'yar hira suna min tambayoyi na shirme ita biye musu domin ni ina son hira da yara don haka naji sun shiga raina domin na lura suna da wayo. Na gama musu fesa musu turare, Meema ta kalli wayata "Momi in ɗauki wayar ki?" Nace me zaki yi da ita? Mubina ta amshe da cewa "Akwai game a ciki?" Nace babu amma ku zo in ɗauke ku hoto mukayi hotuna ni da su. Nace to sai ina? Suka ce za suje gaida Hajiya ne. Nace to ai ni baku gaishe ni ba, suka ce Hajiya ake fara gaishewa sai Dadi shikenan sai mu gaisheki. Nace to haka ya yi daga nan su gaishe min da Hajiya. Suka tafi ina bin su da kallo. Goma saura na saka hijabi na fita, na nufi gurin Hajiya na tsugunna na yi mata sannu da hutawa ta amsa, nace nazo gurin yin aiki. Ta nuna min ƙofa da hannu bi nan zaki samu su Juma a kicin. Hajiya ta bi Baby da kallo cikin wani kallo na nazari, kamar kowace amarya dai haka take zuwa a nuna mata kuxin ƙarshe dai abinci ya ƙi ciyuwa, ta taɓa baki bari dai mugani, domin ta lura yadda abubuwa ke faruwa a safiyar yau ana samun ɗan banbanci da wanda suka faru a matan da Shamaki ya aura, a safiyar farko misali in ya bar gurinta ya nufi ɗakinsa don ya shirya ya tafi kasuwa ya kan ɗauki lokaci bai fito ba, haka ma dai a wannan karon, ya ɓata fiye da awa ɗaya sai dai banbancin da ta lura da shi shine fitowar wannan karon akwai banbanci da na sauran, a yanayin sa a fili yana cike da nishaɗi da kamanin angwaye, sannan kayan da ya saka ta tabbatar ba zaɓin shi bane domin tasan a guri ɗaya yake saka babbar riga shine in zashi wani taro. Tace Allah ya sa dai a dace. Ta miƙe domin yin sallar walha. Ƙaton kicin na riska kuma na zamani ta window kuma na hango wani kicin ɗin na gargajiya inda wasu mata su uku suke ta aiki. Juma kuma tana ɓarar magi, na yi mata sannu ta ce "Amarya kin fito?" Nace e, tace "Muje in nuna miki an gama suyar kaji, wannan ma magin fefe ɗin da za'a yi ne na ke barewa." Nace Sannun da aiki, Mukaje na gani na yi musu sannu. Suka ce Me za a dafa?" Naja Juma gefe nace me ki ke ganin Hajiya tafi so a taro? Tace "E to tunda kin tambaye ni zan faɗa miki, muna yi shinkafa jalaf, tuwo, da alala, waina sinasir funkasau da sauran su, amma yanzu kin ga babu maganar waina ko sinasir, tuna da ba a tashi yin su ba yanzu ko ba gaskiya ba, sai dai a ƙara da wani abin." Nace in akwai kayan ɗanwake za mu iya yinsa, da kuma dambu da funkason ko kina ganin mutane ba za su so su ci waɗannan ba? Tace "Yannan ki ke maganar ba za su so shi ba,ai yanzu babu abinda ke kwantai in dai abinci ne. Muna da ɓarjajiyar shi kafar dambu sai dai bata da yawa sosai, in kuma na kuskus za ayi to." Cikin sauri nace A'a za a yi shi haka ai ko ɗanwake ba mai yawa sosai za ayi ba, na tare maganar kuskus ne domin ban taɓa yin na kuskus ba. Tace 'To ki faɗi gaba ɗaya abinda muke buƙata wanda babu sai a kaiwa Hajiya list za ta aike ni in siya." Na ɗan yi shiru, sai dabara ta faɗo min nace tuwo da kayan shinkafar ki lissafa ki fidda wanda babu, ni kuma sai in lissafa miki na dambu da ɗanwake. Nayi haka ne dan su nafi iyawa. Haka dai muka tada lissafin tuwo za ayi miyar ganye da agushi shinkafa soyayya sai alala da funkaso dambu da ɗanwake. Haka dai aiki ya rincaɓe mana danma suna da hanzarin kuma komai an ɗora wasu akan gas ga kuma murahu. Ina yi ina addu'a Allah ya fidda ni kunya ƙarfe ɗaya da rabi komai ya kammala sai tuwo da suke ɗauewa a leda Gida ko ina ya ɗauki kamshi. Gaskiya su Juma sun iya girki kuma sun taimaka min sosai. Suka ce inje tunda kwashe tuwo ne ya rage in sun gama sai su kai inda aka jere komai. Hajiya tana salla a. Falon ya soma cika da Jama'a yaranta duk sun iso da 'yayansu, na rusuna na gaida kowa sannan na nufi gefe na. Maman Nana tana cewa yanzu Maman Iman ke cigiyar ki. Nace ina kicin ina take? Tace tana salla, na ce nima bari inyi sallar Na shiga ɗaki zan shiga wanka sai naga wayarta a kan gado, sai lokacin na tuna da wata waya, na ɗauka dan in duba ko an kira ni. Kiran Shamaki yafi goma ga saƙo na fara duba saƙunan, magiya ya ke in naga kiran shi don Allah in kira. Cikin rawar hannu na danna kiran shi tana shiga ya ɗaga. Baby lafiya? Nace lafiya Lau, ina kicin muna aiki ne,ban tafi da wayar ba. Yace "Ko ina ki ke Baby ki zama da wayarki a hannu, na manta zaki yi mana girki, kinji yadda hankali na ya tashi ne kaɗan ya rage in taho gidan." Nace da ka kira Hajiya zata faɗa maka cewa ina kicin. Yace "Taɓ to ya za'ayi in iya kiran Hajiya in tambaye ta ke, akwai buƙatar ki lura da abubuwan da basu kamata ba. Ya ki ka san zata kalli abin?" Na yi shiru domin banga wata matsala game da hakan ba to kullum sai Hajiya ta yi abinda na sha mamaki. Yace "Tunda kina lafiya shike nan, dama dai inji muryar ki ne, yau na zama cikin yawan tuno ki da miki addu'a. Kin dasa wani abu a zuciyata iya jiya zuwa yau, dan Allah Baby kar ki canza ta min yaya. Kowa ya ganni a kasuwa sai ya yaba da kayan da ki ka zaɓa min kuma kin san abin mamaki na taɓa saka kayan amma banji wanda ya ce na yi kyau ba sai yau, har waɗanda ba su san na yi aure ba da sun ganni sai suce kamar ango." Cikin mamakin irin zuba zance da Yaya ke yi nace naji daɗi sosai da na saka a farin ciki, insha Allahu bazan taɓa canzawa ba, yin hakan fa dai-dai ya ke da juyawa aljanna baya. Yace me ki ke yi yanzu? Nace wanka zanyi inyi salla sai na shirya fita filin taron. Sai kawai naji subba ta ratsa kunne na ta cikin waya,ta bi sassan jikina wanda haka ya tilasta min sulalewa na zauna a kan gadon tare da kumshe ido. Na ɗago waya na kalla baya sautin ya katse layin . Cikin sanyin jiki na shiga wanka. Bayan nayi salla yau ma dai kwalliya ce aka caɗa min na ci leshi ina ta ƙamshi su Jamila sunzo da su Umman Amina har da maƙotanmu da yawa abu mamaki,dangin Abba ma sunzo. Wani ƙaton fili ne a gidan an shirya shi kamar tantin larabawa. An zuba kujeru a gaban kujerun na alfarma Hajiya tare da wasu manyan Hajiyoyi ƙawayenta suna zaune a kai kusan su goma dukkan su kowa tana ji da kanta. Sai layi na biyu 'yayansu ne. Sannan sauran mutane da abokan arziƙi a sauran kujerun wanda teburi ke tsakiya. Kamar yadda Maman Umar ta shigo ɗakina muna zaune, tace matar waliyina Umma su Zuhra ita ce ta riƙo ni har gaban su Hajiya. Haka aka yi, ina durƙusa na gaishe su, suka amsa cinkin isa da ƙasaita. Sannan Na duƙusa na gaida yayun mijina, aka kaini wata kujera da aka tanadar min. Wata malam ta tashi ta fara gabatar da nasiha game da zaman aure, biyayya ga miji, bin uwar miji, bin dangin miji tsafta iya girki da sauran su. Sai dai banji inda ta faɗi yadda ya kamata uwar miji ta mutunta matar ɗanta ba,dangin miji su girmama matar ɗan uwansu ba,haka banji ta yi magana game da hakkin mace akan miji ba,amma tayi magana sosai akan haƙƙin miji akan matarsa. A zuciya ta nace ko ina dai yanzu mutane suna kare abincin su ne suna yin abinda suka san shine fitar su. Bayan an gama MC ta sanar cewa yanzu lokacin cin abinci ne wanda amarya ta dafa kuma zata fara gabatarwa a gaban Hajiya, amma kafin haka sai ta ɗan ɗana dukkan abincin da ta dafa, sannan za a kai ga Hajiya da Aminanta. Yin hakan ba wai ana zargi ba ne al'adace. Gabana ya faɗi na tashi na nufi gurin da aka jere kayan abincin kowa ya kallona, na zaci su Juma zasu zo su taimaka min amma sai na ga kawai kowa kallona yake yi. Na ɗauki tire na jera plate huɗu suka cika shi na zuba shinkafa nasa tuwo a ɗaya na saka dambu a ɗaya sai kuma na sa Alala a ɗaya, na kuma jera huɗu ɗaya mai zurfi sa matsami na tsamo ɗanwake na zuba a mai zurfin. Sai na zuba kaji da kifi da naman rago. Colsow kuwa shima madubi daban sai na zuma a karamin plate na sa cokali na ɗiba na sa a baki ina ci, sai naji an kwashi tafi. Duk a ruɗe nake, na ɗauki tiren na soma kaiwa ina jerewa a teburin gaban su Hajiya. Sai da na cika teburin komai na zuba musu, lemuka dai dama na ga anjere su da ruwa a kan kowane tebur. Na koma na ci gaba da zubawa, anan ne Juma suka zo suna miƙawa teburin su Maman Umar zuwa na sauran jama'a. 'Yan unguwarmu da yake a ko ina sai an nuna halin, nan suka fara zuwa suna cewa Baby a bamu. Juma ce ta kore su, ta ce kowa ya koma mazaunin shi zai samu. Bayan an gama da manya sai Mc Ta sanar cewa Amarya ta koma nata mazaunin yanzu masu rabon za su zo su raba. Wata mata tare da 'yan mata suka shigo suka soma rabon abincin ni kam Idanuna da hankalina suna kan teburin su Hajiya har zuwa lokacin da mutane suka fara cin abinci ta irin su ba'a fara ba, sannan yanayin kallon da wasu aminan ta suke min ya sa jikina yin sanyi, a zuciya ta kuwa addu'a nake Allah ya fiddani. Kusan kusan mutum uku suka fara cin abincin sannan lura d Hajiya i ta fara ci, sai dai wani abin ban iya gane ko ya ta ji abincin yadda take komai cikin ƙasaita. Masu hotuna da bidiyo ana ta ɗauka gaskiya ni tsarin ya yi min, wata zuciyar tace tunda kin tsallake Hajiya ta ci kyace abin ya birge ki mana. Haka dai aka ci aka sha sannan aka gama. Aka kai wa Hajiya abin magana zata yi jawabin godiya amma kafin haka sai ƙawarta Hajiya Zulaiha ta amsa ta isar da saƙon Hajiya game da abincin da amarya ta ciyar da su, tace "Zan yi ɗan bayani kaɗan kafin Hajiya ta yi godiya, gaskiya amarya girki ba laifi amma a ƙara gyara hannu sosai, ta ɗan taɓa baki, ya yi daɗi sai dai ɗan gyara guda biyu dazan miki, na farko ɗanwake mai da yaji ne sai kika bamu da miya. Na biyu kin mana ɗan zubi a dambu sai ki ƙara sakin hannu kaɗan saboda rowa bata da wani amfani kuma bata cikin sunnar gidan nan. Na sunkuyar da kai, ina mamaki amma duk da haka ni ce da godiya tunda ƙorafin ya tsaya a haka,,Hajiya ta ci abinci Allah ya soni ni. Hajiya ta amshi abin magana tayi godiya ga kowa tare da fatan duk za su koma gidajen su lafiya.Sannan ta sa albarka tare min fatan zama jarumtar mace musamman gurin yi wa miji biyayya. Aka abin maganar wai ince wani abu bani wai nima in yi godiya. Gabana yana faɗuwa na amsa. Nace Mun gode Allah ya maida kowa gida lafiya, kuma insha Allahu zan yi amfani duk shawarwarin da aka bani zan kiyaye. Haka taro ya tashi kowa na san Barka. Ana tashi aka kira la'asar. Hajiya ta kirani inyi sallama da baƙinta. A lokaci ne wannan mai cewa ina da rowar same ta tana cewa "Hajiya Zeena duk matan da ke Kano amma Shamaki ya rasa wadda zai ɗauka sai wannan cokokuwar ko cikin 'ya 'yanmu ya kasa zuwa ya duba. Na kalli Hajiya lokacin da takecewa "Bar ɗan yau da abinda ya ke so Hajiya Zaliha. Wani mugun so ya ke yiwa yarinyar nan ba domin na samu tabbacin ba asiri suka yi masa ba da a haka zan kalli abin. Gaggawa fa ya yi aka je aka nemo masa auren ta. Ni kuma kinsan matsala ta, ina son ɗana da yawa kuma ya rayu akan samun duk abinda ya ke so, in ba ɗana abinda ya ke so matsawar yin hakan ba saɓon Allah bane." Nace su sauka gida lafiya na juya raina ba daɗi, na soma jin takaicin kushe min halitta da ake yi. Gefena tanƙam da 'yan uwa da 'yan unguwa sai kallo na suke suna min murna. Na zauna bakin gado Jamila ta zo ta ce "Abinci ya yi daɗi Yaya Baby kuma ke ki ka dafa?" Na ce e mana. Wayata ta soma ringin ta miƙo min. Na amsa Mijina ne Hajiya ta hana ni faɗa masa Yaya To bansan wane suna zan saka masa ba. Na ɗaga, yace " Yaya Baby gaske ne ke kika dafa abincin nan?" Cikin shagwaɓa na ce wai don Allah nice Yaya? Yace "Ina son yadda su Jamila suke faɗa ne." Abicin bai yi daɗi bane ko? Na tambaye shi. Yace "Inji wa, ai in faɗa miki abincin Hajiya ne kaɗai ya fi naki daɗi." Na yi murmushi a zuciya ta nace ai ita Hajiya komai nata ya fi na kowa. "Sannu soyayyata ,kin yi ƙoƙari sosai. ..... Da na dawo zan shige zan shige gurina sai naji kukan yara, sai na samu kaina da nufar gurin su. Rahin ta yi musu wanka tana ta fama da su zata sa musu kaya amma Mubina bata son kayan da aka ciro musu, ita leshi za a sa mata, Anisa kuma ba wannan takalmin take wa kuka ba, sai an canza. Meema tana kicin kicin saka nata kayan. na shiga nace me ya same su? Cikin girmamawa Rahin ta ce Rigima suke jin yi Anty kinga ga kaya wai kowccen su bata so." Na ce to ki barsu kowa ta ɗauki wanda ta ke so mana ina ganin ai kamar ba matsala ko? Rahin ta ja baya tace "To ku zaɓa amma don Allah kar ku zubo kayan domin shirya su ba ƙaramin aiki bane durowa uku, aiki ne." Nace kije kusa sai su nuna miki sai ki ciro wa kowaccen su yadda ba zai ɓaci ba ko? Ta ce "To " Yara suka bini da kallo sannan suka kasa nuna wanda suke so. Nace In zaɓo muku? A tare suka ɗaga kai. Na dubi Rahin anko ake yi musu kullum?. Tace "Wani lokacin suna sa daban daban." Nace Hajiya tafi son su sa kaya iri ɗaya? Tace "Ban taɓa jin Hajiya ta yi magana akan haka ba ." Na kama hannun su suka nuna min duk abinda suke so, nace to muje ɗakina sai in shirya ku a can. Da sauri suka yarda suka bini Rahin ta bini da kallo. nace ki gyara musu kayan kawai. A Kan gadona nace su hau Meema tace "Hajiya ta hanamu tace gadonmu kawai zamu hau amma banda na manya." A raina nace tofa! Sai nace ai Hajiya bata nan kuma ni bazan faɗa mata ba. Sai suka kalli juna, Mubina ta zau a kan kafe ɗin gaban gado, Meema ta ce "Hajiya ta faɗa mana in bata nan Allahnta yana nan, kuma zai ganar da ita inhar muka yi ba daidai ba. Na sauka kan Kafet ɗin batare da na sake magana ba, nace bari a fara shirya Anisa ita ce 'yar ƙarama ko? Meema ta ɗaga kai, sannan tace "Anty ke ɗin wacce ke ma nan gidan ki ke?" Nace ni Mominku ce, ba sunana Anty ba. Mubina da Anisa duk suka kalle ni , Mubina tace "Kema a nan gidan ki ke?" Nace e mana ga ɗakina ma. "Kece Momin da Dady yace zaki zo in anyi biki?" Inji Meema. Nace la! ashe ya faɗa muku, to ni ce. Anisa tace "To Momy anyi bikine?" Nace anyi jiya yau ma za ayi. Suka fara murna." Na gama shirya su muna ta 'yar hira suna min tambayoyi na shirme ita biye musu domin ni ina son hira da yara don haka naji sun shiga raina domin na lura suna da wayo. Na gama musu fesa musu turare, Meema ta kalli wayata "Momi in ɗauki wayar ki?" Nace me zaki yi da ita? Mubina ta amshe da cewa "Akwai game a ciki?" Nace babu amma ku zo in ɗauke ku hoto mukayi hotuna ni da su. Nace to sai ina? Suka ce za suje gaida Hajiya ne. Nace to ai ni baku gaishe ni ba, suka ce Hajiya ake fara gaishewa sai Dadi shikenan sai mu gaisheki. Nace to haka ya yi daga nan su gaishe min da Hajiya. Suka tafi ina bin su da kallo. Goma saura na saka hijabi na fita, na nufi gurin Hajiya na tsugunna na yi mata sannu da hutawa ta amsa, nace nazo gurin yin aiki. Ta nuna min ƙofa da hannu bi nan zaki samu su Juma a kicin. Hajiya ta bi Baby da kallo cikin wani kallo na nazari, kamar kowace amarya dai haka take zuwa a nuna mata kuxin ƙarshe dai abinci ya ƙi ciyuwa, ta taɓa baki bari dai mugani, domin ta lura yadda abubuwa ke faruwa a safiyar yau ana samun ɗan banbanci da wanda suka faru a matan da Shamaki ya aura, a safiyar farko misali in ya bar gurinta ya nufi ɗakinsa don ya shirya ya tafi kasuwa ya kan ɗauki lokaci bai fito ba, haka ma dai a wannan karon, ya ɓata fiye da awa ɗaya sai dai banbancin da ta lura da shi shine fitowar wannan karon akwai banbanci da na sauran, a yanayin sa a fili yana cike da nishaɗi da kamanin angwaye, sannan kayan da ya saka ta tabbatar ba zaɓin shi bane domin tasan a guri ɗaya yake saka babbar riga shine in zashi wani taro. Tace Allah ya sa dai a dace. Ta miƙe domin yin sallar walha. Ƙaton kicin na riska kuma na zamani ta window kuma na hango wani kicin ɗin na gargajiya inda wasu mata su uku suke ta aiki. Juma kuma tana ɓarar magi, na yi mata sannu ta ce "Amarya kin fito?" Nace e, tace "Muje in nuna miki an gama suyar kaji, wannan ma magin fefe ɗin da za'a yi ne na ke barewa." Nace Sannun da aiki, Mukaje na gani na yi musu sannu. Suka ce Me za a dafa?" Naja Juma gefe nace me ki ke ganin Hajiya tafi so a taro? Tace "E to tunda kin tambaye ni zan faɗa miki, muna yi shinkafa jalaf, tuwo, da alala, waina sinasir funkasau da sauran su, amma yanzu kin ga babu maganar waina ko sinasir, tuna da ba a tashi yin su ba yanzu ko ba gaskiya ba, sai dai a ƙara da wani abin." Nace in akwai kayan ɗanwake za mu iya yinsa, da kuma dambu da funkason ko kina ganin mutane ba za su so su ci waɗannan ba? Tace "Yannan ki ke maganar ba za su so shi ba,ai yanzu babu abinda ke kwantai in dai abinci ne. Muna da ɓarjajiyar shi kafar dambu sai dai bata da yawa sosai, in kuma na kuskus za ayi to." Cikin sauri nace A'a za a yi shi haka ai ko ɗanwake ba mai yawa sosai za ayi ba, na tare maganar kuskus ne domin ban taɓa yin na kuskus ba. Tace 'To ki faɗi gaba ɗaya abinda muke buƙata wanda babu sai a kaiwa Hajiya list za ta aike ni in siya." Na ɗan yi shiru, sai dabara ta faɗo min nace tuwo da kayan shinkafar ki lissafa ki fidda wanda babu, ni kuma sai in lissafa miki na dambu da ɗanwake. Nayi haka ne dan su nafi iyawa. Haka dai muka tada lissafin tuwo za ayi miyar ganye da agushi shinkafa soyayya sai alala da funkaso dambu da ɗanwake. Haka dai aiki ya rincaɓe mana danma suna da hanzarin kuma komai an ɗora wasu akan gas ga kuma murahu. Ina yi ina addu'a Allah ya fidda ni kunya ƙarfe ɗaya da rabi komai ya kammala sai tuwo da suke ɗauewa a leda Gida ko ina ya ɗauki kamshi. Gaskiya su Juma sun iya girki kuma sun taimaka min sosai. Suka ce inje tunda kwashe tuwo ne ya rage in sun gama sai su kai inda aka jere komai. Hajiya tana salla a. Falon ya soma cika da Jama'a yaranta duk sun iso da 'yayansu, na rusuna na gaida kowa sannan na nufi gefe na. Maman Nana tana cewa yanzu Maman Iman ke cigiyar ki. Nace ina kicin ina take? Tace tana salla, na ce nima bari inyi sallar Na shiga ɗaki zan shiga wanka sai naga wayarta a kan gado, sai lokacin na tuna da wata waya, na ɗauka dan in duba ko an kira ni. Kiran Shamaki yafi goma ga saƙo na fara duba saƙunan, magiya ya ke in naga kiran shi don Allah in kira. Cikin rawar hannu na danna kiran shi tana shiga ya ɗaga. Baby lafiya? Nace lafiya Lau, ina kicin muna aiki ne,ban tafi da wayar ba. Yace "Ko ina ki ke Baby ki zama da wayarki a hannu, na manta zaki yi mana girki, kinji yadda hankali na ya tashi ne kaɗan ya rage in taho gidan." Nace da ka kira Hajiya zata faɗa maka cewa ina kicin. Yace "Taɓ to ya za'ayi in iya kiran Hajiya in tambaye ta ke, akwai buƙatar ki lura da abubuwan da basu kamata ba. Ya ki ka san zata kalli abin?" Na yi shiru domin banga wata matsala game da hakan ba to kullum sai Hajiya ta yi abinda na sha mamaki. Yace "Tunda kina lafiya shike nan, dama dai inji muryar ki ne, yau na zama cikin yawan tuno ki da miki addu'a. Kin dasa wani abu a zuciyata iya jiya zuwa yau, dan Allah Baby kar ki canza ta min yaya. Kowa ya ganni a kasuwa sai ya yaba da kayan da ki ka zaɓa min kuma kin san abin mamaki na taɓa saka kayan amma banji wanda ya ce na yi kyau ba sai yau, har waɗanda ba su san na yi aure ba da sun ganni sai suce kamar ango." Cikin mamakin irin zuba zance da Yaya ke yi nace naji daɗi sosai da na saka a farin ciki, insha Allahu bazan taɓa canzawa ba, yin hakan fa dai-dai ya ke da juyawa aljanna baya. Yace me ki ke yi yanzu? Nace wanka zanyi inyi salla sai na shirya fita filin taron. Sai kawai naji subba ta ratsa kunne na ta cikin waya,ta bi sassan jikina wanda haka ya tilasta min sulalewa na zauna a kan gadon tare da kumshe ido. Na ɗago waya na kalla baya sautin ya katse layin . Cikin sanyin jiki na shiga wanka. Bayan nayi salla yau ma dai kwalliya ce aka caɗa min na ci leshi ina ta ƙamshi su Jamila sunzo da su Umman Amina har da maƙotanmu da yawa abu mamaki,dangin Abba ma sunzo. Wani ƙaton fili ne a gidan an shirya shi kamar tantin larabawa. An zuba kujeru a gaban kujerun na alfarma Hajiya tare da wasu manyan Hajiyoyi ƙawayenta suna zaune a kai kusan su goma dukkan su kowa tana ji da kanta. Sai layi na biyu 'yayansu ne. Sannan sauran mutane da abokan arziƙi a sauran kujerun wanda teburi ke tsakiya. Kamar yadda Maman Umar ta shigo ɗakina muna zaune, tace matar waliyina Umma su Zuhra ita ce ta riƙo ni har gaban su Hajiya. Haka aka yi, ina durƙusa na gaishe su, suka amsa cinkin isa da ƙasaita. Sannan Na duƙusa na gaida yayun mijina, aka kaini wata kujera da aka tanadar min. Wata malam ta tashi ta fara gabatar da nasiha game da zaman aure, biyayya ga miji, bin uwar miji, bin dangin miji tsafta iya girki da sauran su. Sai dai banji inda ta faɗi yadda ya kamata uwar miji ta mutunta matar ɗanta ba,dangin miji su girmama matar ɗan uwansu ba,haka banji ta yi magana game da hakkin mace akan miji ba,amma tayi magana sosai akan haƙƙin miji akan matarsa. A zuciya ta nace ko ina dai yanzu mutane suna kare abincin su ne suna yin abinda suka san shine fitar su. Bayan an gama MC ta sanar cewa yanzu lokacin cin abinci ne wanda amarya ta dafa kuma zata fara gabatarwa a gaban Hajiya, amma kafin haka sai ta ɗan ɗana dukkan abincin da ta dafa, sannan za a kai ga Hajiya da Aminanta. Yin hakan ba wai ana zargi ba ne al'adace. Gabana ya faɗi na tashi na nufi gurin da aka jere kayan abincin kowa ya kallona, na zaci su Juma zasu zo su taimaka min amma sai na ga kawai kowa kallona yake yi. Na ɗauki tire na jera plate huɗu suka cika shi na zuba shinkafa nasa tuwo a ɗaya na saka dambu a ɗaya sai kuma na sa Alala a ɗaya, na kuma jera huɗu ɗaya mai zurfi sa matsami na tsamo ɗanwake na zuba a mai zurfin. Sai na zuba kaji da kifi da naman rago. Colsow kuwa shima madubi daban sai na zuma a karamin plate na sa cokali na ɗiba na sa a baki ina ci, sai naji an kwashi tafi. Duk a ruɗe nake, na ɗauki tiren na soma kaiwa ina jerewa a teburin gaban su Hajiya. Sai da na cika teburin komai na zuba musu, lemuka dai dama na ga anjere su da ruwa a kan kowane tebur. Na koma na ci gaba da zubawa, anan ne Juma suka zo suna miƙawa teburin su Maman Umar zuwa na sauran jama'a. 'Yan unguwarmu da yake a ko ina sai an nuna halin, nan suka fara zuwa suna cewa Baby a bamu. Juma ce ta kore su, ta ce kowa ya koma mazaunin shi zai samu. Bayan an gama da manya sai Mc Ta sanar cewa Amarya ta koma nata mazaunin yanzu masu rabon za su zo su raba. Wata mata tare da 'yan mata suka shigo suka soma rabon abincin ni kam Idanuna da hankalina suna kan teburin su Hajiya har zuwa lokacin da mutane suka fara cin abinci ta irin su ba'a fara ba, sannan yanayin kallon da wasu aminan ta suke min ya sa jikina yin sanyi, a zuciya ta kuwa addu'a nake Allah ya fiddani. Kusan kusan mutum uku suka fara cin abincin sannan lura d Hajiya i ta fara ci, sai dai wani abin ban iya gane ko ya ta ji abincin yadda take komai cikin ƙasaita. Masu hotuna da bidiyo ana ta ɗauka gaskiya ni tsarin ya yi min, wata zuciyar tace tunda kin tsallake Hajiya ta ci kyace abin ya birge ki mana. Haka dai aka ci aka sha sannan aka gama. Aka kai wa Hajiya abin magana zata yi jawabin godiya amma kafin haka sai ƙawarta Hajiya Zulaiha ta amsa ta isar da saƙon Hajiya game da abincin da amarya ta ciyar da su, tace "Zan yi ɗan bayani kaɗan kafin Hajiya ta yi godiya, gaskiya amarya girki ba laifi amma a ƙara gyara hannu sosai, ta ɗan taɓa baki, ya yi daɗi sai dai ɗan gyara guda biyu dazan miki, na farko ɗanwake mai da yaji ne sai kika bamu da miya. Na biyu kin mana ɗan zubi a dambu sai ki ƙara sakin hannu kaɗan saboda rowa bata da wani amfani kuma bata cikin sunnar gidan nan. Na sunkuyar da kai, ina mamaki amma duk da haka ni ce da godiya tunda ƙorafin ya tsaya a haka,,Hajiya ta ci abinci Allah ya soni ni. Hajiya ta amshi abin magana tayi godiya ga kowa tare da fatan duk za su koma gidajen su lafiya.Sannan ta sa albarka tare min fatan zama jarumtar mace musamman gurin yi wa miji biyayya. Aka abin maganar wai ince wani abu bani wai nima in yi godiya. Gabana yana faɗuwa na amsa. Nace Mun gode Allah ya maida kowa gida lafiya, kuma insha Allahu zan yi amfani duk shawarwarin da aka bani zan kiyaye. Haka taro ya tashi kowa na san Barka. Ana tashi aka kira la'asar. Hajiya ta kirani inyi sallama da baƙinta. A lokaci ne wannan mai cewa ina da rowar same ta tana cewa "Hajiya Zeena duk matan da ke Kano amma Shamaki ya rasa wadda zai ɗauka sai wannan cokokuwar ko cikin 'ya 'yanmu ya kasa zuwa ya duba. Na kalli Hajiya lokacin da takecewa "Bar ɗan yau da abinda ya ke so Hajiya Zaliha. Wani mugun so ya ke yiwa yarinyar nan ba domin na samu tabbacin ba asiri suka yi masa ba da a haka zan kalli abin. Gaggawa fa ya yi aka je aka nemo masa auren ta. Ni kuma kinsan matsala ta, ina son ɗana da yawa kuma ya rayu akan samun duk abinda ya ke so, in ba ɗana abinda ya ke so matsawar yin hakan ba saɓon Allah bane." Nace su sauka gida lafiya na juya raina ba daɗi, na soma jin takaicin kushe min halitta da ake yi. Gefena tanƙam da 'yan uwa da 'yan unguwa sai kallo na suke suna min murna. Na zauna bakin gado Jamila ta zo ta ce "Abinci ya yi daɗi Yaya Baby kuma ke ki ka dafa?" Na ce e mana. Wayata ta soma ringin ta miƙo min. Na amsa Mijina ne Hajiya ta hana ni faɗa masa Yaya To bansan wane suna zan saka masa ba. Na ɗaga, yace " Yaya Baby gaske ne ke kika dafa abincin nan?" Cikin shagwaɓa na ce wai don Allah nice Yaya? Yace "Ina son yadda su Jamila suke faɗa ne." Abicin bai yi daɗi bane ko? Na tambaye shi. Yace "Inji wa, ai in faɗa miki abincin Hajiya ne kaɗai ya fi naki daɗi." Na yi murmushi a zuciya ta nace ai ita Hajiya komai nata ya fi na kowa. "Sannu soyayyata ,kin yi ƙoƙari sosai. ..... Yace "Yawwa Baby amma Hajiya ta ci abincin kuwa?" Nace ta ci mana har ƙawayenta duk sunci. Ya ce to Alhamdulillah! Allah ya yi miki albarka me ki ke so in zo miki da shi?" Na yi ƙasa da murya kai kawai nake son ka dawo lafiya bana son komai. Sai kurum na ji sumba a kunne na tare da faɗin ina sonki da yawa zan faɗa miki wani abu amma don Allah kar hakan ya sa ki canza min." Nace ka faɗa min Allah bazan taɓa canzawa ba. Yace "Baby idan yadda nake ji a game da ke shine soyayya, to a baya ba soyayya na yi ba, duk bugun numfashi sai na tuno ki,na samu kaina da hirar ki da kowa harma da waɗanda ba su kamata inyi hirar da su ba. Don Allah Baby kina jin makamancin abinda nake ji?" Na sauke ajiyar zuciya, zanfi son in faɗa maka idona yana kallon na ka, in ka dawo wannan hirar za muyi. Ya kuma sumbatar wayar ba tare da ya kuma cewa komai ba ya katse wayar. Na zurawa wayar ido ina farin ciki. Zuwa biyar duk aka watse sai su Jamila suka ƙara gyara min ko ina fes ita da Amina na ɗauki kuɗin da abokansa suka bani na ba Jamila nace ta kaiwa Umma duka dubu Ashirin ne. Tace "Ki aje goma a hannun ki a kai mata goma saboda ko za kiyi baƙi zaki iya ba su kuɗin mota." Nace to haka ne. Na basu turare da janbaki daga cikin kayan lefena ita da Amina, su Jafar ma. turare na basu suka min sallama suka tafi. Na yi wanka nayi sallar magariba na saka wani farin leshi mai ratsin gwal na sha turaruka ina jiran mijina. Sai dai har nayi sallar Isha'i aka kawo min abincin dare amma babu labarin angona na ɗan dai ci farfesun kajin da farar shinkafa kaɗan domin naji yunwa, da rana ban iya cin abinci ba. Na sake gyara fuskata na zuba ɗaurin ɗan kwali na zauna ina kallon TV, na aje turare a gefe na da zummar in ya ƙwanƙwasa ƙofa infeshe jikina da shi kafin in buɗe. Can cikin bacci naji bugun ƙofa Lokacin ina mafarki ina gida gamu tare da su Umma. Na tashi firgigit ɗankwalina ya faɗi na ganni a ɗaki na naje na buɗe ƙofa shine tsaye ga jakarsa a rataye. Na zuga hamma sannan nace masa sai yanzu ka dawo sannu da zuwa, Na miƙa hannu zan amshi jakar hannunsa Yace a a barta zomuje ɗakina." Nace bari in yi shirin kwanciya. Yace 'a 'a muje haka." Na juya na ɗakko ɗankwalina ya kulle ƙofar da makulli. Da ƙyar na ke tafiya na gaji liƙis saboda aikin da muka sha ɗazu kuma ni ina da wata ɗabi'a in na fara bacci aka tashe ni raina ɓaci ya ke ga ciwon kai. A Ɗakin nashi na kalli agogon bango ɗaya da minti biyu. Na zauna bakin gado ya shiga banɗaki, a zuciya ta nace haka zai ta zama a gurin Hajiya Kullum har irin wannan lokacin? Taɓ da sake na furta a zuciyata. Na kwanta a kan gadon inajin futowarsa ya yi wanka ya gama feshe feshen turaren sa, na yi laf ni a dole bacci ya kwashe ni.Ya zo ya shafa gefen kumatuna ya na faɗin "Baby." Na sake jan bargo . Ya min magana a kunne wai Baby ki tashi ki saka kayan bacci. Sai na yi kamar zan tashi sai in kuma ɓingirewa, ina jin sa yace Baby kinsha gajiyar aiki ne bari dai in haƙura nima yau. Ya jani jikinsa,. hardai , baccin gaske ya ɗauke ni. Yauma kamar jiya zai tafi masallaci ya tashe ni, haka nan shiru bai shigo ba bisa dukkan alamu yauma sai zai tafi kasuwa, to kenan bani da wani lokaci da zamu zauna da mijina muyi hira wannan babban ƙalubale ne a tare da ni ya zama dole in nemo wa kaina mafita, sannan ya kamata in kula sosai gurin nemo mafita kar in nemo wadda zata fiddani daga gida. Yau ya kamata in fara bugar cikin Juma domin insan ina nasa gaba a gidan. Na gyara ko ina a sashen sa sannan na dawo na gyara nawa, na karya na yi wanka sannan naje gaida Hajiya. tace "Ya baƙunta?" Nace Hajiya ai na zama 'yar gida. Ta "'A 'a har yanzu ke baƙuwa ce tunda baki gano lokacin da ya kamata ki gaisa da mutanen gida ba sai rana ta hudo ki ke iya fitowa Ina fatan dai ba sai yanzu shima Ubangiji aka gaida shi ba?" Na matsa kusa da ita na sunkuyar da kai ina ɗan murmushi, ba yanzun bane, tunda zai fita ya tashe ni, nan ɗinne dai Allah bai sa na zo akan lokaci ba, ina neman afuwa akan hakan. Ta ɗan taɓa baki tace "Ko kusa ba kiyi laifi ba gidan aurenki ne nan dole ki huta in sautin ki ka zaɓa." Na sunkuyar da kai Nace, akwai abinda za ayi muku ne? Tace a a babu komai,.kije ki sallami mijinki mana." Na sunkuyar da kai ina zaton yana shirya wa ne domin tafiya kasuwa. Tace "In ya gama ai dole zaku yi sallama ko?'" Na miƙe tare da faɗin To Hajiya. Ina sane na yi musu haka sai da ya shiga na zo gaisheta dole nima in nemi mafita ta akan wannan lamarin, amma ina da buƙatar sanin wasu abubuwa. Zan tashi sai ga su Meema cikin shirin makaranta. Suka durƙusa har 'yar Anisa suka gaida Hajiya. Nace kun gama shirya wa. Suka kalle ni sai suka ce Hajiya ina Dady?.Tace "Yana ciki kuje da sauri ku gaida shi karfa ku jima ku dawo yanzu ku tafi." Azima ta shigo itama cikin kayan makaranta ta gaida Hajiya sannan ta nufi ciki kenan zata gaida mijina. Na miƙe tare da faɗin to bari inje. Hajiya ta ce Allah ya yi albarka. Ina shiga falonsa na samu yaran suna ta wasa Azima ta ƙwanƙwasa ƙofar ɗakinsa. Na dube ta sai naji wani kishin ta ya kamani, nace Ke ɗan jira mana ta tsaya. Nace zauna bari ya fito. Tace "Za muyi latti." Yadda ta yi maganar ya nuna itama akwai alamun kishin. Nace bari ya fito yanzu. Ya gama shiri tsaf cikin farar shadda, ya ce "Yau ba a zo an bani kaya ba." Nace naje gaida Hajiya ne. Ya janyo ni jikin sa, "Jiya kinyi bacci kin barni nasan gajiya ce." Nace na gaji sosai, kuma inna yi bacci aka tashe ni dama ciwon kai nake yi ,jiya Allah ya taimake ni kaina baiyi ciwo ba da ka tashe ni, ko da yake na koma baccin da wuri. Yace "To saboda me?" Nace ban sani ba, amma ƙila domin bana yin baccin rana ne. Yace "To kinci bashin na jiya yau za'a maida min. Na zaro ido bashin me? yace "Zan faɗa miki inna dawo," Nace yara fa na jiranka a falo. Da sauri ya fito yana faɗin "Za su lattti." Azima ta gaida shi ya amsa tare da tambayar ya yaga fuskarta haka ba walwala. Tace ba komai. Ya ɗauki yaran duk ya sunbace su ya musu addu'a suka rugo gurina "Momy ina kwana?" Na amsa na yi musu addu'a nima. Azima ta gaishe ni na amsa sannan suka fita. Ya kalle ni "Momy yara." Nace na am Dadyn yara. Muka koma ciki muna dariya. Ya zauna bakin gado yana min wani kallo, "Zan tafi kasuwa ina ƙishirwa." Na yi kamar ban gane ba sai nace, Bari a ɗebo maka ruwa mana. Ya ɗauki jakarshi na amsa. Yana faɗin "Ba wannan ba, nace To wanne? Ya lakuci kumatuna "Zaki sanshi inna dawo." Muka fito har ƙofar falon Hajiya na miƙa masa ya ƙi amsa ya shige falon Hajiya ya rusuna ya cire hula ta dafa kanshi tana yi masa addu'a. Ya miƙe na saci kallon Hajiya cikin ɗari ɗari na ce mishi ga jakar. Ita ma ni take kallo, yace "Kin fasa rakani motar ne?" Na kalli Hajiya da sauri, ta ɗaga kai alamun inje,sai na bishi. A falon kusa da waje ya tsaya yace "Da bazaki rako ni ba tsoron me ki ke ji?" Nace inajin nauyin Hajiya ne. Yace Hajiya zataji daɗi taga kina kula da ni yana cikin abinda take dubawa a cikin jarabawarta." Na sunkuyar da kai. Dama kaima kasan Hajiya tana jarabawa? Ya sunkuya ya sunbaci leɓunana, yace "Ki koma daga nan bana son masu aiki su lalle ki, ki zama tare da wayarki zan kira ki." Nace Allah ya tsare ya bada sa'a. Na dawo na durƙusa gaban Hajiya Nace za 'a yi miki wani abu ne? Jin shiru yasa na ɗago na dubeta, ita ma ni take kallo. Na buɗe baki zan yi magana ta ɗora yatsanta akan leɓenta da sauri alamun inyi shiru. Sannan cikin isa ta ce, "Haka ku ke magana kamar kuna yin magana da maƙota? Haka ki ke yi wa ɗana magana? da irin wannan sautin ku ke hira lokacin da ya ke zuwa zance? Na yi shiru ina kallon ta. Ta girgiza kai sannan ta ci gaba da faɗin akwai buƙatar ki sake sabon tsari game da irin wannan hayaniyar da ki ke tsammanin cewa magana ki ke yi." Na kaɗa kai alamun naji, domin ina tsoron kar inyi magana in sake yin sauti mai ƙaran da tace. Tace "Tashi ki je kuma ba ina nufin ki kama baki ki min gum in anyi magana ki kaɗa kai kamar ƙadangaruwa ba." Da leɓuna na amsa ban bari sun fitar da sauti ba. nace To. Na zauna a bakin gadona na yi shiru ina tunani wajibi ne in koyi yadda suke magana domin in samawa kai na sauƙi, amma ta yaya? Wa zai koya min yadda suke magana? Amma kuwa anya ba nau'in wulaƙanci a lamarin Hajiya, shi so ɗaya ya min magana tun yana zuwa zance,kuma daga lokacin na rage sautin muryata in muna magana da shi. Sannan su Juma da yaran ai duk na yi magana da su amma banji wanda ya ce komai game da sauti na ba. Na tuna yadda Hajiya ta wani toshe kunne kamar na kunna mata lasifiƙa, kuma ita ma munsha yin magana da ita kafin yau. To ko yau ɗin na ɗaga murya ne? Na tambayi kai. Koma menene na sha alwashin yadda na shigo gidannan matsawar ba da mijina na samu matsala ba,zan jure komai da komai in samu zama hamshaƙiya kamar yadda ta faɗa. Na yi gyaran murya na soma gwada yadda zan yi magana a gidan da kowa a gidan. Shamaki a kasuwa duk wani kaikawo da wata ganawa da manyan kwastomomin su da ya ke yi sai amaryarsa tana zuciyar sa Allah Allah Allah yake ya ɗan samu dama ya kira ta ya ji muryarta kuma ya tabbatar ta na cikin ƙoshin lafiya. Ina tsaka da gwaji .kiransa ya shigo, a zuciya ta nace Yawwa bari in gwada da shi, na ɗaga na amsa da muryata can ƙasa. Da sauri naji ya ce, "Baby me ya faru? Ba lafiya ne?" Nace a a mekaji? Yace "Muryar ki wata iri." Nace ina koyon yadda zan ke yin magana da ku ne? 🖊️🖊️🖊 ️Ya ce "Kamar yaya kenan? Nace ashe ina ta magana da ƙarfi maimakon ka faɗa min sai ka ci gaba da sauraron a haka sai da Hajiya ta nusar da ni a yau, don Allah ka yi haƙuri, kuma daga yau na saukar da muryata ni ma. Nayi ya yi shiru, can ya ce. "Karki takura kanki zuwa yanzu ni na saba da maganar ki." Ya canza maganar da faɗin "Fatan ki na cikin ƙoshin lafiya." Nace lafiya lau ya kasuwa? Allah ya taimaka. Yace "Ameen. To yauma rana ta uku haka na fuska sai ƙarfe shabiyu ya shigo, ni kuma na yi kwanciya ta na kulle ɗaki, banji bugun sa ba sam. Ban farka ba sai kiran sallar asuba, da na farka na ganni a ɗakina take naji fargaba, ko yaya wannan bawan Allahn zai ɗauki bin oho. Cikin sauri na ɗakko wayata na duba bai kira ni ba, na shiga banɗaki na yi alwala na fito naji ana ƙwanƙwasa min ƙofa. Da sauri naje na buɗe, shine a tsaye zashi massalaci yace " Ashe kin tashi ma toshi kenan na tafi masallaci." Babu wata alama ta damuwa data nuna a fuskar sa. Nace to, dama ka yi ta kirana ne baccin ne mai nauyi banji ba. Ya yi murmushi "Kada ki damu, ban kira wayarki ba ma,saboda zata tashe ki bacci kuma kinga kanki zai yi ciwo yanzu kije ki yi salla nima kada in makara. Na idar da salla na zauna kan sallaya ina tunanin ta ina zan ɓullowa wannan al'amari. Yanzu ma nasan sai zai tafi kasuwa zai shigo ya shirya. Na ɗakko ƙur'ani na zauna ina ta karatu har ƙarfe bakwai, na tashi da sake wani salon dabarar na shiga na fesa wanka na gyara fuska ta na zuba kwalliya na saka Atamfa doguwar riga na ɗaura ɗankwani bayan na saki gashina a kafaɗa. Na fesa turaruka mayafi na yafa kamar mai zuwa unguwa na nufi gaida Hajiya. Suna zaune kamar kullum suna zantuka ƙasa-ƙasa. Nayi sallama can ƙasan maƙogwaro suka amsa na durƙusa na gaida Hajiya ta amsa fuska a sake, sannan na juya na gaida shi ya amsa yana ta kallona, na ɗan zauna jim,sai na dubi Hajiya zan iya zuwa in taya su Juma aiki? Duk suka Kalle ni, ya kalli Hajiya da sauri. Tace "Menene dalilin ki na so shiga kuxin?" Na ƙasa ƙasa da murya, dama dai ina son in koyi wasu abubuwanne waɗanda ban taɓa ya ba. Tace "To sai ki rubuto min abinda baki iya ɗinba kinga sai in sa a koya miki." Na koma gefe na zauna ina kallon su,sai satar kallona ya ke yi da mun haɗa ido sai ya faki idon Hajiya ja ɗaga min gira. Can Hajiya tace. "Kinga tashi jeki iciki kin raba mana hankali muna magana. Na yi mata sallama cikin ladabi sannan na tafi. Ina ta kai kawo a cikin ɗaki ina neman shawarar da zan yanke. Hajiya bazata yarda in zauna kusa da su ba kuma bazata bari in raɓi su Juma ba,ga mijina munyi nesa dole dai in samawa kaina farin ciki na nufi gefen sa ma jiya Rahin da yara ana shirin makaranta,na zarce gurinsu. Ta taga na ke kallon yadda suke shirin, sai na shiga na ƙara gyara musu. Mubina tace "Momy saboda ke momy ce shine ki ke saka mana kayanmu?" Nace e mana ai ita Momy ta son taga yaranta sunyi kyau sosai sun fi kowane yara. Meema tace Zainab ƙawata tace su Momynsu ta ke yi musu Homework mu kuma sai dai Anty lesson take mana. Nace wacece kuma Anty Lesson Rahin ta ce wadda ke zuwa gida tana ƙara musu karatu. Nace au, to ina kuma Azima ta ke? Rahin ta nuna min ɗayan dakin da hannu ta ce ita ga ɗakinta can. Na tashi na nufi ɗakin tana zaune bakin gadon ta tana saka safa, ɗakine sosai irin na mace da komai a ciki. Ta bini da kallo nima dai ita nike kallo zancan gaskiya kuma yarinyar tana da kyau sosai. Nace Azima baki zo ɗakina ba Ni gashi na zo naki, ko bakya son mu saba ne? Taɗan taɓa baki. "Ni bana da ra'ayin sabawa da kowa sai Hajiya kawai." Nace haka ne. Ni kuma nafi sabawa da Shamaki. Ta kalleni da sauri sai kuma ta sunkuyar da kai ta ci gaba da abinda take yi. Nace bari in tafi,in kin dawo zaki zo ɗakina? Tagirgiza kai tare da furta 'a'a. Na tafi ina mamakin 'yar ƙaramar yarinya ta iya kishi haka. Ɗakinsa na koma na shiga gyarawa har na gama bai zo ba, na fito Juma ta dawo daga kai min abinci nace a kawo turaren gefena tace to, har zan tafi sai nace bari injirata domin inyi amfani da damar in ji wani abu a gurin Juma. Ta kawo turare, ta ake zata tafi, nace ni ko Baba Juma dan Allah ina da tambaya, sai naga ta juya da sauri tamkar bata jini ba. Na cika da mamaki na kama hanya na yi ɗakina. Kaina gaba ɗaya ya kulle,sai naji an ƙwaƙwasa ƙofa, ina buɗewa sai naga Juma da turaren gefena tace ai 'yannan na jiki ɗazu kiyi hankali ba ko ina ake magana a gidan nan ba domin cike yake da kyamarori. Na zaro ido tace zan samu wani dalili da zan shigo ɗakin baccin ki a ciki ne ba a saka kyamara. Bata jira jin me zance ba ta wuce. Na koma na zauna daɓas akan kujera, ina tunanin wace irin kyamara, a zuciyarsa nace ƙila irin ta gidan Ya Umar Soja wadda ya sawa Asmy a littafin da na taɓa karantawa na fuska biyu. Ashe dai akwai shi a gaske kenan. To in Yaya Umar Faruk ya saka wa Asmy kyamara domin ya ga abinda take yi in baya nan ko tsoron karya na ƙarta kawo masa namiji gida su kuma nan gidan saboda me suka saka? Dole akwai buƙatar in shiga taitayina sosai, tunda shi kanshi da yake iƙrarin sona bai sanar da ni cewa in kula akwai kyamara ba. Laf na yi a cikin ɗaki a saman gadona, hatta karin na kasa yi, can naji an buɗe ƙofar falona an shigo. Nasan shine domin naji ƙamahinsa. Na tashi zaune yace "Wai har an yaye ni ne?" Nace kamar yaya? Yace baza a zaɓa min kayan ba? Nace to ai kai nake jira, ga mamakina sai yace "To ba sai a ciro a ajiye min ba tunda an gyara min ɗakin." Na miƙe to muje in baka. Ya kamoni zuwa jikinsa, yace "Baby sai inga kamar kina guduna ne, jiya ki ka ƙi zuwa ɗakin mijin ki." Nace Barci ne ya kwashe ni. Ya ɗago fuskata ya haɗa tsinin hancinmu yace "Ba sai kije can ki yi bacci ba?" Na kumshe ido nace yau zan yi haka. A ɗakinsa duk da nayi wanka sai da muka sake yi tare domin sai da ya ja dalilin haka, gaskiya na yarda da son da yake min domin ya nuna min zallar hakan sannan ya iya tafiyar da mace cikin sati ɗaya na amarci bani da bakin magana. Damuwata shine ƙaranci lokacin da muke yi da shi. Duk dare sai nayi bacci yake shigowa, ba bu haduwar asbashi, sai da safe kurum muke soyayyar da bata fi ta minti talaatin ko arba'in ba. Ba hira sam, Lokaci dai da zamu zauna mu yi hira babu shi, ko ya fita kasuwa sai dai in masa text na miƙa gaisuwa amma fa in na jiraci amsa to ni ce zanji haushi, ɗan lokacin da ya kan samu ya kira ni ma ba kullum ba. Ranar da na cika kwana goma sai na tashi da mura da zai fita ya sanar da Hajiya. Tace assha sai an kira likita ne ko kokuwa dai akai mata magani?Yace Ina ganin kawai akai mata magani tunda ta yi aiki ma. Hajiya tace Allah ya sawaƙa. Ina kwance akan gado naji sallamar Juma nace ta shigo ciki, ta kawo min magani muta tace "Hajiya tace ayi miji sannu." Nace ina amsawa. Tace to tace ayi miki sannu in kinji ba wani sauƙi sai a kira likita. Nace ba komai. Tace kwanaki kin ce zaki tambaye ni wani abu." Nace e ta ce "To ga shawara duk wani bayani da za ki so ji in kin kwantar da hankalinki zaki same shi, amma in kin fi son ki tambaye ni to kina iya tambaya amma zance ka iya tasowa in faɗawa Hajiya cewa kin tambaye ni abu kaza, bansanta ba amma hakan ka iya shafar jarabawarki. Ta ƙara matsawa kusa ba a banza ki ka ga na kwashe shekaru a gidannan ba, 'yar amanar gidance dan na yaba da halinki ba shine zai sa in zaɓe ki in buɗe musu sirri ba. Na ɗan taɓaki ne domin ku lura da zaman gidan ba wai domin ni da ke mu zama munafukan Hajiya ba." Tuni na yi mutuwar zaune, amma sai na dake nace, Allah sarki Baba Juma waccan ranar dama zan tambaye ki ne ko zan iya zuwa kicin inke tayaku aiki saboda in koyi wanda ban iya ba, to kuma na riga ma na tambayi Hajiya tace in rubuta abinda zan koya sai ta sa a koya min. Juma ta ce "Allah Sarki to ai Hajiya baza ta yarda ki shiga kicin ba, domin Hajiya bata yarda ɗanta ya ci abincin wata matarsa ba. Amfanin ki ɗaya ki biya wa ɗanta buƙata ki haifa masa 'ya'ya. Na danne tsoron da ya taso min nace, to ita matar aure ai bata da yadda zata yi sai abinda mijinta yace. Juma ta juya ta ce ashe dai kin gano." Na bi bayanta da kallo a fili nace akwai aiki. ..... Na koma na kwanta ina tunani, kullum in na kalli sauƙi ta nan sai ya zama tsuri, na tabbatar wa kai na Juma tana sanar da ni ne cewar bata da sirri sam. Ga gida cike da na'urorin ɗaukar hoto. Yawata ta soma ruri, na duba lambar Umma ce, na ɗaga Jamila ce, cikin rawar murya ta ce Yaya Baby Umma ba lafiya gamu zamu tafi asibiti haihuwa ce tun jiya jini ne ya ɓalle mata da sauri na diro daga gado ina faɗin wane Asibitin ne gani nan zuwa. Tace Murtala zamuje. Da gudu na ja hijabi na saka na sa takalmi har na fita daga falo sai wata zuciyar ta tambaye ni da cewa,kin tambayi mijinki? Na ciri wayar a jaka na yita kiran wayarsa amma bai ɗaga ba. Na nufi gurin Hajiya na tsugunna a gaban ta idanuna sun ciko da hawaye. Tace "Jikin ne?" Nace a a ko maganin ban kai ga sha ba, aka kira Ni daga gida Ummanmu za akai asibiti jini ya ɓalle mata. Tace Ya Salam! To yanzu ya akayi? Nace zanje ne. Tace kin faɗawa mijinki? Na dubeta bai ɗauki wayata ba. Tace to kiyi haƙuri ki koma har sai kin samu izni daga gare shi. Na sake rusunawa nace Hajiya ko ku zaku kirashi wallahi bata cikin hayyacita. Hajiya tace "Samu nutsuwa mana Rabi'atu, ki koma ɗakinki ki jira mijinki ya dawo ko ya ɗaga wayarki, ko kinje baki da wani taimako da zaki iya yi mata bayan addu'a ki koma ciki ki yi mata. Na miƙe a hankali hawaye suna tsiyaya daga idanuna, na nufi ciki a hankali kamar kazar da ƙwai ya fashe mata na nufi sashe na. Ina shiga na cire hijabi kaina nayi jifa dashi na na zube nan a ƙasa ina rera sabon kuka tare da kiran dukkan layukan Shamaki amma babu wanda ya ɗaga. Na kira wayar Umma itama Jamilan bata ɗaga ba. Na kira ta Abba shima sai a kira na uku ya ɗauka, cikin kuka nace Abba ta haihu? Yace "Kash waya faɗa miki ba na hana kowa ya sanar da ke ba!" Nace Abba saboda me? Yazun ma saboda baya nan ne shiyasa ban taho ba,amma ya jikin nata? Yace "To a ci gaba da addu'a sun dai shiga da ita ciki har yanzu ba su fito sun ce mana komai ba, sai faɗa suke wai anbarta a gida ta galabaita. Su kuma kowa yasan cewa in ba kuɗi baza su taɓa taɓa mara lafiya ina ta buga bugar neman kuɗinne bansamu na kirki ba gara a gurinta an samu dubu tara." Nace Abba ka turo Jamila ina da dubu goma ta kawo maka su. Yace "Ina ki ka samu karfa kice zaki taɓa kuɗin mijinki." Nace nawa ne abokan sa suka bani Jamilan ma tasan ina da kuɗin tunda agaban su ne aka bani. Yace "To zan turo ta yanzu daga nan Asibitin Murtala sannan karki sake ki fito ba tare da sanin mijinki ba." na. Cikin kuka nace to Abba. Muna aje waya na ɗora sabon kuka ina addu'a. Kamar minti arba'in sai wata wayar tarho da ke maƙale jiki bangon ɗakina kusa da gado ta shiga tsuwa, ni har na tsorata zan fita da gudu na jiyo tsuwa a ɗakin bacci tunda ban taɓa ji ba. Na leƙa na kalli inda nake jin ƙarar sai naga ashe gurin wayar ne, naje na ciro na saka a kunne, muryar Hajiya naji tana cewa "Kece ki ke da baƙuwa a gate? Nace e ni ce ƙanwata ce Jamila. Tace koma waye ba ƙanwarki ba, kamata ya yi ki sanar a faɗawa mutanen da ke gate in ba haka ba baza su barta ta shigo ba. Cikin dasashiyar muryar da na sha kuka nace zan kiyaye gaba insha Allahu Hajiya tace shike nan. Jamila tana shigowa muka rungume juna muka ɗora sabon kuka,kunsan minti uku sannan na lallasheta na ɗakko kuɗin na bata, nace su da waye a asibitin tace Umman Amina ce da Umman su Zuhra, sai Abba. Na rakota zuwa falon Hajiya ta yi wa Hajiya sallama Hajiya tace "Har zata wuce to kin bata ruwa ta sha kuwa?" Nace na shafa'a sauri take daga asibiti ta ke. Jamila na fita zan juya Hajiya tace "To me tazo yi kenan haka?" Nace saƙo na bata. Tace "Amma banga komai a hannun ta ba?" Har zan ɓoye sai na tuna da maganar Juma da ta Shamaki, game da faɗan gaskiya, sai nace kuɗi ne na bata zata kai wa .Abbanmu asibiti. "Ina kika same su?" Ta jeho min tambaya da sauri. Nace abokan shi suka bani ranar da aka kawo ni. Tace "Kin ce abokan shi, shi wa?" Na fara gajiya da tambayoyin ga halin da nake ciki sai na soma hawaye cikin rawar murya nace Shamaki. Ɗa gyaɗa kai tare da faɗin "To na gane, shi kuma kukan na menene?" Na share hawaye tare da girgiza kai nace ba komai. Ta maida kallon ta ga TV na wuce ciki zuciyata fal da takaici. Haka azahar da la'asar suka riske ni a gurin ba wani labari a halin na faɗawa Jamila zan ke kira ina samun labarin halin da Umma take ciki amma kona kira bata ɗagawa. Shima Abba shiru, shikuwa mijina fushi ma nayi ban ƙara gwada wa ba. Addu'o'in dai ba irin wadda bana yi. Sautin wayata ya sa na tashi da gudu na nufi ɗalkota ina dubawa Shamaki ne, na zauna a ƙasa ina kallon wayar harta yanke, ya sake kira har lokacin ban ɗaga ba. Gani nake babu wani amfani ko na ɗaga. Karan da wayar ta addabe ni da shi ya ci gaba da kirai shi ya sa dole na ɗaga amma ban iya magana ba na kara a kunne Yace "Baby Ina meeting a Abuja lokacin da ki ka kirani yanzu ina filin jirgi nan da minti talatin ina Kano me ya faru?" Na saki sabon kuka, cikin muryar da na yi kuka na gaji nace Umma ta mutu ina ta kiranka baka ɗaga ba ƙilama yanzu an kaita. Yace "Wace Umma?" Nace Ummanmu na kashe wayar na ɗora sabon kuka.Ni na gama yanke wa tunda suka ƙi ɗaga wayata bashakka Umma ta mutu na rasa ta har abada. Shamaki ya yi tsam a filin jirgi ya ɗaga waya ya kira Number Abba. Abba ya ɗaga Shamaki ya gaida shi cikin girmamawa, sannan yace "Yarinyar nan ce ta kira ni tana min kuka "Wai da gaske ne Allah ya yi wa Umma Rasuwa?" Abba yace Baby akwai ruɗaɗɗiyar yarinya, shiyasa ban so Jamila ta faɗa mata ba. Kuma shine dalilin da ya sa nace karsu ɗaga kiranta.Ummansu addu'a take buƙata, bata rasu ba yanzu dai sun ce mu tafi asibitin Malam Aminu Kano. Aiki ne za'ayi mata. Shamaki yace Abba ina ganin ku tafi asibitin Zeena Hospital zan sanar da likitan kafin kuje ya ɓuɗe mata fayal. Abba yace alhamdulillah na gode Aliyu Allah ya sa a mizani. Yace ba komai sai munzo asibitin. Ban kuma ji daga kowa ba har magariba.In Kwance inda nayi salla. Juma ta shigo da abinci ta ga na rana yana nan. Tace "yannan ki daure ki ɗan taɓa mana." Nace Baba Juma karki aje haɗa duka bazan iya ci ba. Tace "Banga laifin ki ba yarnan Uwa ta wuce wasa. Kuyi addu'a Allah ya fisshe ta. Nace Ameen. Yau ce ranar farko da na ganshi ya shigo a irin wannan lokacin. Ban Ko ɗago ba bare in dune shi. Ya tsugunna a gaba ya sa hannu ya ɗago ni fuska ta ta yi suntum yace "Subhanallah Baby kinga fuskar ki kuwa? Na soma sabon kuka ya rungume ni ki samu natsuwa, ki shirya muje Asibitin mu duba ta. Nace bata mutu ba? Yace ta samu sauƙi muje ki tabbatar Na tashi da sauri na shiga ciki na wanko fuska na saka Hijabi yace "A' a ki canza shiga mai kyau, sannan ki ci wani abu naji tace haka ki ka yini. Nace zan canza shigar amma abinci kam ka min afwa sai na ga jikin. A falon Hajiya mun rusuna ya sanar da ita cewa mun fito. Tace Juma ta haɗa abincin da za'a kai asibitin. Muka fita tana cewa mu yi mata sannu. Muna baya Bala direba ya na jan mota muna baya ya sarƙe hannuwanshi cikin nawa har muka kai Zeena Hospital. Nace ba Murtala aka ce ba ? Yace "Ƙila daga can aka turo su nan." Muka shiga ni dai da kyar nake cire ƙafa, ban damu da gaisuwar girmamawar da Nurse ɗin ke yiwa Shamaki in mun haɗu da su jifa jifa ba. Ya kira yaawar wani yana tambayar sa da turanci lambar ɗakin. Ya faɗa masa har mun ɗan wuce sai muka dawo baya. Abba na zaune bakin gadon da Umma ke bacci ya riƙe mata hannu da ake yi mata ƙarin jini.Kan tabarma kuma Jamila ce da Umman su Amina. Da sauri naje na riƙe mata hannu Abba ya ce ai bata farka ba ,bayan anyi aikin. Na dubi Abba da sauri nace wai dama aiki aka mata. Ya ce "aiki aka yi mata 'yan ta wahala kukan ta ɗaya da aka ciro ta ta koma ga Allah." Allahu akbar, ina take Abba. Yace "An rufe ta ɗazu nan kafin magriba ita kuma sai mu yi fata Allah ya bata lafiya." Muka amsa Shamaki suka gaida da Abba ya masa ya maijiki daga nan yace zaije ya duba wani ya dawo,ya fita . Abba ya ce ki bi mijinki sau da ƙafa dubi abinda ya yi mana banda shi da sai dai Ummanku ta mutu domin bani da kuɗin da za a yi mata aiki. Na dubi Abba shine ya biya? Abba yace komai da komai. Bala direba ya shigo da kayan abinci Jamila ta amsa ta na yi masa sannu, suka gaida da Abba ya tambayi mai jiki sannan ya fita. Shamaki suka shigo da likitan na gaida shi. Likitan ya yi bayanin cewa saura minti arba'in ta farka anyi aikin cikin nasara kuma zata tashi lafiya lau. Sai yanzu na haɗiye wani tarin abu da ya maƙale min a wuya. A fili na furta Alhamdulillah yace da ta farka kar su bata komai su sanar da shi. Shamaki yace zamu tafi sai kuma gobe zamu sake zuwa. Nace ya barni in kwana,wata tsawa da Abba ya buga min bansan lokacin da a nayi waje da sauri ba. Muna zuwa gurin mota Sahamaki ya ba Malam Bala kuɗi yace ya hau mashin ya wuce gida bari shi ya ja motar zamu biya unguwa ne. Na koma gaba ya ja muka tafi. Kawai gari muka yi ta zaga wa muna hira yana ɗan Min wasanni, mushiga wannan Supar market yace in ɗauki abinda nake so har goman dare sannan muka nufi gida lokacin zuciyata ta yi sanyi ta cika da nishaɗi. Muna shigowa Azima tana shafawa Hajiya maganin ƙafa duk suka bimu da kallo, na ajewa Hajiya ledar hannu na domin naga tana kallon ledar. Tace Menene? Shamaki ya ce turarene mun biya na sayi nawa ne shine na sai muku,ta sa albarka ta tambayi yana yi jiki muka ce da sauƙi. Nan da na barsu na tafi ɗakina. Na yi salloli sannan na shiga wanka na shirya na nufi ɗakin mijina. Washe gari da safe da ya shigo daga gurin Hajiya zai yi shirin kasuwa nace zaka sa a kai ni asibiti ne ko in zaka kasuwa ne zaku sauke ni? Yace jirana ake yi bazanbi ta can ba,amma game da naki zuwa ki tambayi Hajiya inta ce ki je zata sa a kai ki. Na yi sororo ina kallon sa kamar in ce Hajiya nake aure?Sai kuma na fasa na fita zuwa gurin Hajiyar irin tambaya tun yana gidan. Na rusuna na sake yi mata sannu da hutawa, sannan nace Shamaki ne ya ce in tambaya ko zani asibiti? Jin shiru ya sa na ɗago na dube ta itama ni take kallo a zuciyata ta nace kema dai Uwa ce kinsan zafinta. Ga mamaki na sai baki tace ki je ki buga musu yawa kiji lafiyar ta, babu buƙatar zuwanki. Na rusunar da ƙwayar idanuna sannan na miƙe tare da furta to. Ɗakina na koma na zauna a kan gado na ɗora sabon kuka. Ina jin shigowar shi ban ko ɗago na kalleshi ba , ya zauna kusa da ni yana tambayar abinda ke faruwa. Nace ba komai. Yace "Hajiya ce ?" Nace 'A 'a . Ya miƙe tare da faɗin shike nan ni zan tafi kasuwa, na miƙe ina share hawaye na amshi jakar kamar kullum domin yi masa rakiya. ...... Na raka shi har falon ƙarshe ya amshi jakar ya ɗago fuskanta ki daina kuka ya kawo bakin shi kunne na ya raɗa min cewa zanbi ta asibitin zan kira ki in faɗa miki yadda jikin yake kinji?" Nace To kace cewa Umma don Allah ina son zuwa ban samu dama bane ina son in ganta kuma ina yi mata addu'a . Wasu hawayen suka biyo kumatuna, ya sa hannu ya share yace "zan haɗaku da ita a waya. Nace to. Yace "Share hawayen ki" Nasa hannu na share sannan ya fita ni kuma na dawo, zan wuce nace cewa Hajiya sannu da hutawa. Ta amsa da "Yawwa." Haka na koma ciki naci gaba da 'yan ayyuka na. Na gama na koma na kwanta . Gurin ƙarfe goma sai ga kiran shi na ɗaga. Yace gani a Asibiti jikin Umma ya yi kyau sosai ki je video call zan kira ku gaisa. Da rawar jiki na shiga video saiga Umma zaune tana min magana cikin murna na gaishe ta, nace ya jiki? Tace "Jikin da sauƙi Alhamdulillahi ya naki jiki?" Nace na samu sauƙi. Tace "Ki daina kuka akan sai kinzo tunda ba daɗin jikinki ki ke ji ba, sannan ki yi godiya gurin Hajiya surukarki muna ganin aiken abincin safe da yamma Allah ya ƙara ɗaukaka." Nace to zan faɗa mata, yanzu dai babu inda ya ke miki ciwo? Ta ce. " Babu inda ke min ciwo Baby ki kwantar da hankali ki, ki ƙaraiwa mijinki godiya ya taimaki rayuwata sosai." Nace To Umma. Muka yi sallama. Naji daɗin ganin Umma ta sami sauƙi kuma ko da Hajiya ta hanani zuwa ashe tana aika musu da abinci, sannan bata hana mijina zuwa ba ya duba Umma ba. Kwanan Umma uku a asibiti aka sallameta amma Hajiya bata barni na je ba, koda yake ban tambaya bane ina jin tsoro, da nace zanje sai ya ce in tambayi Hajiya. Ni kuma sai in yi shiru bana sake maganar , kuma ko a fuska bana nuna wata damuwa. Amma kira inna kira su sai munyi waya da kowa a gidan har su Jafar. Na dangana na zubawa sarautar Allah ido. Ranar da zata cika sati ɗaya da 'yar tana raye sai a ce ranar suna, 'yan Kurna za su zo da ƙawayen ta za'ayi ɗan taro. Jamila ce ta tsegunta min gaskiya ina son zuwa dan haka tun yau na rubuta mashi saƙo cewa ina son gobe zanje gida in duba Umma saboda za 'a yi ɗan taro. Shina amsa ya aiko min da ita kamar kaka..." Ki je ki sanar da Hajiya." Na yi shiru cikin tagumi Hajiya ke aure na da komai zai ce in tambayi Hajiya. To shi mai zai hana ya tambayar min. Na danna kiranshi. Ya yanke ya kira ni. Na ɗaga. Nace ya kasuwa? Yace "Alhamdulillah" Nace dama zance ne ko zaka tambaya min Hajiya ɗin wallahi ni sai inke jin tsoro kar ta ga kamar na matsa mata. Yace "Baby haka dokar gidan ta ke, ke zaki tambaya da kanki in taga ya dace shikenan zata barki, har yau baki fahimci Hajiya bane shiyasa ki ke jin tsoronta. Ki tashi yanzu kije ki same ta ki faɗa mata uzrin ki, in ta yarda shike nan." Nace To bari in gwada, mu kayi sallama. Lokacin ƙarfe uku zata yi domin an yi azahar. Na sameta tana karatun wani ƙaramin littafin. Na durƙusa na gaisheta sannan na ce Hajiya dama ina son in tambaya ne ina son inje gida in duna Umma da jikin ta, goben ta ke kwana bakwai. Ta ɗago kai ta ce za tayi taro kenan? Nace 'yan uwanta ne zasu taru. Ta yi shiru na ɗan lokaci sannan tace "Mijin ki zaki tambaya Ni menene nawa?" Nace ai na tambaye shi yace min duk abinda ki ka ce shi za'ayi. Ta sauke ajiyar zuciya "Kira min Juma." Da sauri na miƙe domin kiran Juma. Tare muka shigo, tace "Juma dubi yarinyar nan sosai ki gani ta canza daga yadda ta zo gidan nan Ni kullum juya iyau na ke ganinta?" Juma tace ta canza gaskiya ta murje ta yi haske Hajiya ai dole a canza kinsan hutu daban ya ke. Hajiya ta dube ni. "Jeki Allah ya kaimu goben zan duba in gani inzaki samu zuwa. Na ce to, ko fuska ban canza ba har naje ɗaki. To ranar ma dai Shamaki bai dawo ba, daga can wai ya tafi Lagos sai text ɗinsa na gani, wai tafiyar gaggawa ce .Lamarin ya fara sani tunanin ko dai ba wani so da mutumin nan yake yi min. Bana samu wata kulawa da na ke buƙata in nayi la'akari da yadda na ke karantawa a littafai, ko 'yan unguwar mu da na kan ga sun fita da mazajen su irin da da dare haka suna ɗan zaga gari suna shan iska. Ni gani a kulle ba aikin fari ko na baƙi, bani da ko sisi sai dai inyi kallo in ci insha, ko hira mu yi da mijina ta gagara har yau bansan abinda ya fi so ba, shima bai san abin da na fi so ba ko wanda bana so ba . Da safe bayan na gama komai naje na sake rusunawa gaban Hajiya nace dama na zo ne inji ko in shirya? Ta dube ni, "Kin faɗawa mijinki? ". Nace tun jiya yace in kin amince sai inje. Ta ce to yau kun gaisa da shi?" Nace 'A 'a, da sauri tace "To saboda me mijinki baya gari amma baki kira shi ba?" Na daburce nace na kira bai ɗaga bane shine na aika mishi saƙo. Tace "Karantamin saƙon inji." A zuciya ta nace iko sai Allah. Na ɗauki wayar na fara karantawa. Fatan ka tashi lafiya,na kira ka baka ɗaga ba,nasan kana cikin uzri dama dai zan gaishe ka ne, fatan zaka dawo lafiya Allah ya bada abinda aka je nema. Ta dube ni tace "Ameen" Kin kyauta sosai ki yi ta yi wa mijinki addu'a, sai dai ba irin ɗan sunan nan na ku na zamani yadda zai ɗanji sanyi da irin "yan kalamai haka masu daɗi? Na sunkuyar da kai. Hajiya dai son kanta ya kai inda ya kai.Na faɗa a zuciya, a fili kuma nace, zan gyara insha Allahu. Tace "Yawwa ai gara a gyara ɗin. Kije ki shirya sai direba ya kai ki, ƙarfe nawa zaki dawo?" Cike da murna nace duk lokacin da kika ce . Tace ki zama cikin shiri daga ƙarfe biyu zai koma ya ɗakko ki. Ina fita falon na sheƙa da gudu ɗakina harda rawa ina ɗiban shoki tsabar murna. Na shirya tsaf cikin shigar Atamfa. Gaskiya na ɗan ciko komai nawa ya ɗan ƙaru. Na fito falon Hajiya na zauna a gefe. Ta dube ni. "Antyn zumuɗi har a shirya kenan, to inga jakar me zaki kaiwa Ummar ta ƙi?" Nace miƙa mata tare da faɗin ba komai zandai je in ganta. Ga mamakina sai naga ta caje kakar sai 'yar hoda ta ce sai tissue. Ta miƙo min jakata. Sannan ta ce Haka" zaki gidan hannu rabbana?" Nace to ai Hajiya Ni bani da abinda zan ba su. Tace Ai abin kunya ne kina auren mai kuɗi kamar Shamaki amma kije gida hannu na dukan cinya haka, ba daɗi ai kyanshi ace kinje jakar nan cike da kuɗi duk wanda ya halarci taron sai ki bashi wani abu." Take zuciyata ta faɗa min cewa Hajiya tana da wata manufa a maganar ta. Nace to ni kuwa Hajiya ina zan samu kuɗi har in yi hakan? Tace "Ga Mijin ki da kin kira shi sai ya tura miki ta account ku biya da direba ki cire." Na sunkuyar da kai ina ta nazarin maganar Hajiya duk da cewa sak ta yi maganar kamar daga ranta, amma sai najii a jikina cewa Hajiya tana sane ba domin Allah ta yi wannan maganar ba. Ta katse min tunani da cewa "Ki kira shi mana." Nace Hajiya ni ko account ɗin ma bani da shi,,kuma banda haka ma yaya za 'ayi yana irin wannan wahalar ko isasshen lokacin kansa baya da shi amma sai inkirashi ya bani kuɗi ba tausayi kenan, inda ace haka ake yi Hajiya da ba'a kawo haka ba. Mu gode da irin ɗawainiya ta kai abinci Allah ya saka a mizani, suma suna ta godiya su Umma da Abban. Ta zura min ido,can tace shike nan ki shiga ɗaki na zakiga wata leda a saman gado na ki ɗakko min." Nace to, na miƙe ita kuma ta ɗauki waya tana kiran layin direba. Yau ne ranar farko da na fara shiga ɗakin baccin Hajiya, wani mugun ƙamshi ya bugi hancina. Sai dai ban tsaya kallo komai ba, domin ina tsoron ko akwai kyamara.. Amma fa ɗaki ne na alfarma. Na durƙusa na miƙa mata nace gashi. Tace "To tunda kinƙi tambayar shi ni ga tawa gudummawar nan ki bata Allah bata lafiya. Na faɗa miki tun daga ƙarfe biyu sai ki shirya ki jira zuwan direba kar yazo a barshi yana ta jira." Nace sanyi duk yadda ki ka ce Allah ya saka da alkhari. Na fito tasa Juma ta ɗauki ledar ta kai mota sannan na fita,sai da na tabbatar gani zaune a mota sannan na kira Jamila ta wayar Umma nace gani a hanya. Sai naji ta kwashi ihu da murna na kashe wayar na jefa a jaka,,sannan na buɗe ledar inga abinda ke ciki. Turmin atamfa guda biyu, sai wata farar Envelope na buɗe kuɗi ne 'yan ɗari biyu rafa ɗaya. Tabbas zargina ya tabbata Hajiya latsa ni ta yi . Tabbas sai na zama mai kula domin na fuskanci Hajiya ta iya latsin basira. A bakin lungun gidanmu ya tsaya, ya fito ya bude min ƙofa, sannan na fito ya amshi ledar ya biyo ni. Kamar na taka da gudu in isa gida haka babu,amma sai na tafi sannu saboda direba da ke biye da ni cikin girmamawa. Na amshi ledar na yi masa godiya sannan na shiga da sallama, kamar taron suna gida ya cika, ban ko tsaya amsa gaishe gaishe ba na nufi ɗakin Umma da gudu tana zaune a kan gado sanye da atamfar ankon bikina. Na zauna bakin gado na kama hannun ta ina sannu Umma. Sai fara'a ta ke yi tana kallo na. Na gaishe ta na tambayi jiki sannan na gaida sauran mutane. Sai faɗi ake yi amarya tubarkaalla. Umman Amina tace ya surukar ki kuwa? Ai mun taho muna hirar ta wannan mata tana da kirki kuwa? Na yi murmushi nace tana da kirki sosai kuwa. Na ɗakko laidar nace gashi ma tace a kawo wa Umma. Nanfa kuma aka shiga yaba mata. Jamila ta kama hannu na muka shiga ɗakinmu na da muka zauna,tace "Yaya Baby wai don Allah kina da ciki ne?" Nace ke Jamila yaushe ki ka zama haka? Tace "Ba wai yaushe na zama haka bane, kinsan dai nice abokiyar shawara,nace bani da komai me ki ka gani? Tace "Kinyi kyau." Nace danma baya samun zama Jamila kinsan ko hira bamu taɓa yi ba,amma karki faɗawa Umma. Tace "Kamar yaya ko hira ba ya kwana a gidan kenan?" Na bata labari dai dai da fahimtar ta. Tace "To kinsan me za kiyi?" Nace 'a'a tace da rana kisha bacci da dare ki tashi ki dire ki ce bakya jin bacci shima ki tsare shi da hira." Nace Gaskiya Jamila kina da kwanya, amma kuma zan tausaya mishi ai in har zaije da rana ya sha wahalar kasuwa dare kuma in hana shi ya huta. Tace Hajiyar ta rage mishi lokacin lissafin da ranar ko da daren mana. ..... Nace Jamila kenan, zan gwada Allah ya sa dai kada hakan ya zama wata matsalar a gidan kinsan komai a gidan ɗan ƙa'ida ne. Jamila tace "Ameen insha Allahu ba wata matsala, yanzu dai nasan za'a canza miki waya, ina riƙon taki, ko kiba ni 'yar dubu biyar in sai mai botura." Nace ina naga kuɗin da zan baki, kinsan Allah banda kuɗin nan da Baba ya aiko ki kika ki ka karɓa da sai in ce miki ni ban taɓa ganin takardar kuɗi a gidan nan ba. Shi kanshi ban taɓa ganin kuɗi wai yau gashi a hannun shi ba. Jamila ta saki baki tana kallo na. "Dama duk kirarin kuɗin basu a zahiri kenan suna ɓoye a banki?" Nace to ƙila hakanne. Tace "Rannan wata 'yar Ajinmu tana labarin Gidan Hajiya Zeena da irin dukiyar da ke danƙare a gidan wai 'yan uwansu ne. Na ce mata ni yayata a gidan ta ke aure. Da farko ta ƙaryata wai Ɗan Alhaji Baita ba zai auri 'yar gidan mu ba. Shiru na yi mata sai da wasu 'yan ajinmu suka tabbatar mata shine ta yarda,tace gaskiya ta dangwalo, ance gidan suna da ɗakin kuɗi ko ƙananan yaran gidan sai dai su shiga su ɗiba, sannan Makka duk wata." Na kwashe da dariya nace kai mutane Allah ya kyauta. Jamila ta ce "Dama ni na musa wannan labarin amma ina kokwanto nace bari dai zan tambaye ki inji tunda na san dai ke yanzu kinsan komai." Na kauda zancan da faɗin, tashi ki rakani gidan su Zuhra mu gaisa da su. Umman su Zuhra tace "A 'a ,ga fa amare muka gaisa ta tambayi Hajiya nace tana lafiya duk tace a gaida ku. Tace ai wannan mata daga gani zaki sha ɗani a gurin ta, sam mace ba rahma magana ma da kyar a ke yinta ita dole ga mai kuɗi." Nace la kuma Umma sauƙin kai ne da ita dan baki zauna da ita bane. Hajiya ba ruwanta wallahi. Ta taɓa baki, "To kenan mu ta wulaƙanta? Nace ta yi muku wani abu ba daidai ba ne? Tace "Koda yake ke kina rufe radda muka kai ki. Kallo ma bamu ishe ta ba, bare washe gari da muka koma." Nace ikon Allah ƙila dai ko mutane ne suka mata yawa kin san shi'anin taro. Haka dai na yi ta kare Hajiya domin ko iyayena bazan bari su ji sirrin zama na da Hajiya ba, kar in ɗaga musu hankali,ko kuma su zo suna jin haushin ta. Jamila ma sai da nayi mata kashedi domin kar ta faɗa.Na san kuma bazata faɗa ba. Muka dawo ana ta raha duk wata budurwa ta lungun mu da taji labarin na zo sai ki ganta wai tazo mu gaisa. Kamar yadda Hajiya tace daga ƙarfe biyu in shirya haka na yi, ina yin azahar na shirya ina jira direba. Jamila tana ta mita wai maimakon in kai dare. Nace ana wanke tukunya dan tuwon gobe ne, bazai yiwu in wuce lokacin da aka bani ba. Da naga uku ta kusa na kira Hajiya na gaisheta cikin girmamawa na haɗa ta da Umma ta yi godiyar saƙo, sannan na tambaya ko direban ya iso. Tace "Aka ta aike shi ne in ya dawo zai zo. Sai biyar da wani abu ya iso,muka kama hanya zuwa gida. Umma dai citta da daddawa ta bani wai in kaiwa Hajiya. Na kai mata nace inji Ummanmu tace "To an gode jeki kaiwa Juma. Na kai mata kicin ta ce amarsu ansha gida kin dawo da wuri ko Hajiyarmu ce ta baki lokaci? Na yi ɗan murmushi nace sai anjima. Tace kinga a nan babu wannan na'urar hakan yana ɗaya daga cikin abinda zai sa Hajiya ƙi ta barki ki zo nan ɗin. Nace kalle ta ban yi magana ba. Taci gaba da faɗin "Ko da yake jimawarki a nan shima abin tuhuma ne a gurin Hajiya. Na yi 'yar dariya nace Baba Juma kina da abin dariya wallahi. Tace 'yar nan da baƙin wayo ki ke, kin ƙi ki ɓara dan kar ince kin yi munafircin Hajiya ko? To sha mutumin ki, Hajiya bata amsar magana sai da hujja ba bugar cikin ki zanyi ba. Nace ni Bab Juma bana gane irin waɗannan zantukan. Tace "Ba wani bakya gane wa, daga ganin waɗannan wayayun idanuwan naki kar ki ke kallon kowa. Ni dai na fice, zan nufi gefena. Hajiya tace "Basa cikine naga kin jima? Nace suna ciki munyi magana ne. Tace to madallah. Ƙarfe sha biyun dare ina kwance a tafkeken gadon Shamaki ina ta ninƙaya, ina son in gwada hikimar Jamila ne in tsare shi da hira. Na ɗauki wayata ina shirin tura masa saƙo cewa yau dai ina jiransa hira na ke son mu yi.Sai kawai naga saƙonsa kamar haka. "Baby ban samu dawowa ba ƙila ma ba gobe ba, amma zan sanar da ke in zan dawo. In kin kira ni baza ki same ni ba,amma ni zan kira ki a duk lokacin da na samu dama." Na karanta na sake karantawa. A fili nace tofa! Ni wai dama wannan ne auren da mata ke cewa Allah ya kai su gidan hutu su yi aure su huta? Hummm gaskiya kam ina hutawa in dai bacci da cin abinci da nama shine hutu. Na sauka a gadon na nufi ɗaki na na kwanta. Ban sake ji daga mijina ba sai bayan kwana biyu ina zaune shiru zama ya ishe ni, na tashi na nufi sasan su Mubina, sai ina jiyo hayaniyar su a wani guri. Nabi hanyar sai na riski wani ɗan gurin shan iska da 'yar rumfar gargajiya, ga lilon yara sannan gurin akwai ni'imar bishiyu. Suna ta wasa can kan wata kujera Azima ce tana karanta wani littafi na Hausa. Nace Azima kuna nan kuna shan iska kenan? Ta ɗago ta lalle ni haka sama-sama tace "Umm." Ta maida kanta ga karatun. Na isa gurin su Meema nace ku daina wasa kuzo in koya muku karatu kuna s? Duk duka ce e, suka biyo ni nace muje ɗakin karatun ku inda Antynku ta lesson ta ke koya muku, ni na islamiyya zan muku. Muna tsaka da karatu daga izifi biyu muka fara zuwa ƙasa. Sai waya ta tayi ƙara,na ɗaga da sauri ganin Shamaki ne. Na yi sallama na ce sannu. Ya amsa. Tare da faɗin Baby gaskiya ki samin suna kafin na dawo in kin ɗaga waya sai dai ki dinga wani kame kame abinda zaki kirani da shi. Nace to zan nemo amma ka taya ni mu zaɓa. Muka gaisa,yace "Abubuwa na sai kinyi haƙuri kinji?" Ina son ki fa Baby karki zata bana sonki." Nace nasani ,yace yanzu kina ina? Nace ina nan tare da yarana. Yace to haɗa ni da su." Na dubi Meema na ce ga Dady. Ta amshi wayar tana murna ta ce Dadynmu yaushe zaka dawo?" Yace "Duk lokacin da na gama abinda ke gabana zan dawo." Tace a kawo mana tsaraba. Yace to ba mubina ita ma mu gaisa. Ta amsa tace Dady ga mu a gurin Momy muna yin karatun ƙur'ani Momy ta iya karatu mai daɗi. Yace to ku dage ku yi sosai zan kawo muku tsaraba." to zaka kawo wa Momy yace "E ita momy ai babbar tsaraba zan kawo mata sabuwar Baby kuna so?." Tace Muna so Dadi Ya ce "To ana Anisa ita ma." sun gaisa kafin daga bisani na amsa. Yace sannu Malama Baby Allah ya bada sa'a." Nace wai yaushe zaka dawo ne? Ni fa na.. sai na yi shiru,yace "Faɗa min kinyi me?" Kin ƙosa in dawo?" Na ce E "Kina kewata kenan?" Na ƙara ƙasa da murya nace E. Yace "To zaki daina jin kunya ki yi min duk abinda nace kimin ina so?" Nace amma banda ɗayan, cikin shagwaɓa na yi maganar. Yace "Wanne a ciki ne baki so?" Nace ba nace maka ina jin kyama ba?" Yace shikenan ni kuma shi nafi son shi.. zan koya miki amma ki daina jin kyama banda abinki Baby akwai wani abu da zai baki ƙyama a tare da ni? Nace ka ga akwai yara dama zaka kira anjima. Yace "Yanzu na ɗan samu dama Baby. Nace to zanyi. Yace "Kin ɗauki alkawari? " Nace zan dai yi ƙoƙari in ga ko zan iya. Yace "To ki shirya na faɗa wa yara zan zo da tsarabar Babynmu sabuwar jaririya kin shirya? Na ce Duk yadda Allah ya yi fatanmu dai mu samu masu albarka. Yace "Amin, to bari in barki ku yi karatun ku ko? Nace To Na gode. Cikin dare ina bacci kiranshi ya tashe ni, a tsorace na ɗaga wayar" yace "Nasan kin yi bacci kuma na yi laifi na tashe ki, gobe zan dawo Baby a matse nike gida zan wuto don Allah ki shirya. Nace to ba damuwa. Da safe da naje gaida Hajiya nace mata gashin kaina ya yi datti ina son inje gurin wanke wa. Ta saki ɗan murmushi, "Mijinki zai dawo ko? To haka yana da kyau ina ki ke wanke wa?" Nace sai dai ko in yiwa Maman Iman magana wadda ke min a gida ne can Unguwar mu. Tace ba damuwa zan faɗa mata sai direba ya kai ki. Nace To. Na koma ɗaki ina mamaki. Tun takwas aka ce in fito. Aka kai ni wanki kai aka min baƙin lalle zuwa sha ɗaya da rabi na zama tsaf,sai da na dawo na karya. Hajiya ta dama wani abu a cikin madarar shanu ta aiko min. Cikin ikon Allah na shiga ban ɗaki zan yi alwala azahar sai ga baƙon mata ya riga shi zuwa. Na zaro ido. kai tsaye gida ya nufo lokacin ƙarfe ɗaya dan haka ya aiko da kaya ya shiga Masallaci. 🖊️🖊️🖊️ Tamkar kazar da ƙwai ya fashe wa a ciki haka na koma. Falon Hajiya na nufa lokacin da Juma ta zo ta ce Hajiya tace a sanar da ni mijina ya dawo. Har zan ce ki ce ina yi masa sannu da zuwa sai na ji Juma ta yi wata magana, tace kema dai makar sauran ce a faɗa masa kina yi masa sannu da zuwa. Masa sannu da zuwa?" Nace 'a'a ina zuwa dai zaki ce Baba Juma, Yaya mijina zai dawo tafiya ta kwanaki a kira ni kuma in aika da saƙon sannu? Tace "Ashe dai kinsan kan ki. Ta fice wannan ɗin duk cikin jarabawa ce, ki na gani kamar ba gaske bane ko?" Bance komai ba ta fice. Na tashi Na je gaban madubi na dubi leshin jikina ya yi kyau, na shafa janbaki na ɗaura ɗan kwali na baza gashin zuwa kafaɗa ta tunda na san yana son gashin. Na fesa turaruka sannan na nufi falon Hajiya cikin taku irin na matar so. Ya na zube gaban Hajiya kamar zai mata sujjada nan kuma ga Juma nata fito da kaloln abinci, wani daɗi naji ya rufe ni da na ganshi, na nufeshi ina fara'a ina faɗin sannu da zuwa ka sha hanya. Ya zuba min idanu har na zo kusa da shi na tsugunna. Yace bazan amsa ba sai na ji sunan, na kalli Hajiya sannan na fara gaishe shi, ya amsa tare da kai hannu ya shafi gashina, na sake kallon Hajiya da sauri sai naga ita murmushi ma ta ke yi. Na zauna sannan nace ko in sa maka abincin ne? Yace "Da kin kyauta amma fara bani ruwa." Na buɗe murfin robar ruwan na cika tambulan na niƙa mishi, sannan na ce wane abinci zaka ci a ciki?" Ya dire kofin yace duk abinda ki ka ga ya dace Baby ni zanci." Na kuma kallo Hajiya yanzu kam idanuwan ta suna kan talabijin amma na tabbatar kunnan ta yana tare da mu. Nace zan fi so ka zaɓa amma tunda ka bani zaɓi zance ka ci tuwo ƙila shine tunda kaje can baka ciba. Yace "Gaskiya banci tuwo ba, kuma yana cikin abincin da nake so. Na zuba masa komai da farfesun kaza sai zoɓo. Yana ci ina ɗan danna waya ta shi kuma yana satar kallo na da mun haɗa ido ya ɗaga min gira. Yace amma ke kinci abincin ko?" Nace sai anjima yana ɗaki. Ya yanko lomar tuwo da cokali ya nufo baki na, ki ci anan daga nan ɗakina zamuje ki ɗan matsa min jikina na gaji da yawa. Na kalli Hajiya har yanzu bata tare da mu a ido amma a kunne nasan tana ji. Na buɗe baki na amsa, sannan nace to ya isa haka ban jima da karyawa ba, kai dai ka ci sosai yanzu ka dawo daga tafiya. Yace na ci da yawa, to ke ma ki ɗan ƙara ko so ɗaya ne, ya kuma miƙo min, na amsa nace. To na gode. Yace "Rama min za kiyi ki daina faɗin wani kin gode." Nace wannan mai sauƙi ne yana cikin aiki na da zaka bani dama in kullum ka ke son in baka abinci zan fi ka murna domin dai nice da ƙaruwar. Muryar Hajiya ta katse ni da faɗin "ƙaruwar me?" Na sunkuyar da kai nace Lada na ke nufi Hajiya. Ta kuma ɗauke kai. Na fara ba shi a baki ina satar kallon Hajiya, tamkar bata san muna gurin ba. Zan bashi Lemon zoɓo ya min cakulkuli na gantsare saura kaɗan in saki kofin cikin dariya nace zaka sani in saki kofin in yi ɓarna. Na je kusa da kunnan sa, nace ka bari Hajiya tana kallo fa. Yace "Hajiya wai kina kallo? Kin gani Mamanmu ce bazata hana mu yi wasa ba ko Hajiya?" Ta dube shi. "Me ka ke cewa? Yace "Wai kunyarki ta ke ji." Ɗan tsaki ta yi sannan tace ku daina sani a shirmen ku ina kallon wani shiri ne a gidan Talabijin. Haka dai yana ta tsokana ta har muka gama, yace mu tafi ciki. Har mun wuce Hajiya ta kirani, ta miƙamin wata ƙaramar ƙwalbar zuma mai kyau, tace "ki yi amfani da wannan. Kinsan ya ake yin amfani da shi? Na girgiza kai alamar 'a 'a. Tace "Ki sa auduga ki ɗiba sai ki yi matsai kamar minti biyu sai ki cire." Na.sunkuyar da kai dan kunya nace to. A ɗaki ina shiga ya hau rawar jiki, nace akwai damuwa fa. Ya tsaya yana kallona nace bana salla. Ya ƙara jana jikinsa ya ce "Karki yi min haka bazan jure irin wannan wasan ba." Nace ba wasa bane bari in nuna maka. Yana gani na ga duk yanayin sa ya canza ransa a ɓace. Nace in akwai wani abu da zai sa ka samu nutsuwa zanyi maka. Yace ke da ki ke kyamata." Nace ai na bari. To haka dai ya sa nayi ta yi masa wasu abubuwa har sai da ya samu nutsuwa. Duk abin da na ke faɗin ina ƙyamar dole na yi masa saboda ya bani tausayi. Bacci ya kwashe mu sai kiran magriba ya tashe mu. Yace "Subhanallah! ba mu yi la'asar ba. Tare muka yi wanka muka yi la'asar sannan ya fita Masallaci. Haka dai zaman ya ci gaba da tafiya duk wanda ya ganni abin sha'awa amma bani da ko ƙarfanfana jiki na ya yi lukui ƙamshi ya kama jikina saboda irin turarukan da Hajiya ta ke bani farko na zargi Hajiya ko kishi take yi da matan ɗanta har ta ke korar su, amma abin ɗaure kai shine, Hajiya bata da wani buri sai in yi abinda zai sa ɗanta ya ji daɗi. Da kanta take bani maganin mata, kitso da ƙunshi kuwa da ya fita zata sa a kuma yi min wani. Sannan kullum in na zo gaishe ta nasiharta shine in farantawa mijina rai kuma in masa biyayya, in jure duk yadda ya zo min domin in kare shi daga matan waje. Abubuwan da take bani ina sha sun kai matsayin ni da kaina na ke ƙosawa mu yi auratayya da shi. Haka nan zuwa yanzu duk wani abu da ya ke so na gama gogewa da iya su, har ma nakan tambaye shi ya 'akayi ya iya duk waɗannan abubuwan. Sai yace min koya ya yi shima a karance karance. Kwatsam wata safiyar Lahadi baya fita kasuwa da wuri, yana falon Hajiya ni kuma ina gyaran sasan shi. Sai naji ƙarar shigar saƙo a wayarshi na kalli wayar,, gargaɗin da aka min ya faɗo min, amma sai na watsar na ɗauka na janyo saman inna zan iya ganin saƙon sai naga ta Whatsapp ne, an turo Video ne kuma sunan sai naga an saka NFS. Bansan dalili ba sai naji gabana ya faɗi, an yi min nasiha sosai akan waya kowa faɗa ya ke yi min in kiyayi wayar mijina. Dan haka sai na aje. Amma tun daga ranar na tattara hankalina sai da na gano cord ɗin wayar. Bayan kwana biyu sai na sake samun dama yana wanka na buɗe kai tsaye na shiga Whatsapp ɗin sa. Na yi searching wannan sunan sai ya fito min da chat ɗin su, duk da cewa da turanci suke magana kuma gaskiya ni bana fahimtar turanci sosai amma na gane hirar ta batsa ce ya goge Videos amma naga inda ya yi taggin yana faɗa mata cewa hoto ya yi kyau. Motsin sa ya sa na aje wayar na ci gaba da abinda na ke yi. Na yi ta kallon shi ina mamaki matukar mamaki. Ga wata tafasa da zuciya ta ke yi. Ya kalle ni, "Babyna ya aka yi ne?" Na ƙaƙaro murmushi kyau na ga ka ƙara wallahi ina kishinka kamar wasu matan suna sonka a waje. Ya yi 'yar dariya "Baby ke dai Allah ya kyauta amma mata yanzu ai ba'a raba su da son maza, suma mazan haka." Nace Yawwa dan Allah to ina son ka buɗe min Whatsapp ka ga duk 'yan makarantar mu suna yi, ina son muna zumunci. Ya ɗan haɗe fuska, yace "Ki bari sai na canza miki waya tukuna." Nace to Allah ya baka iko. Yace Ameen Baby na,ya saki fuska. Na raka shi yadda na saba na dawo na shiga ɗakina na soma sabon kuka, ina cewa wai me ya kai ni ne, me yasa na dubo wa kai na damuwa. Amma naji mamaki wai Aliyu Shamaki shine ke neman mata! Duk da haka ban daddara ba yana bacci na saci wayar na shige ban ɗaki na gama duba duk wasu mata da yake soyayya da su. Mata ne masu aji kyawawa sun fini komai, wani abin takaici harda wasu mata 'yan Film. Tambaya ta ita ce da wane lokaci ya ke samun haɗuwa da su? 🖊️🖊️ Bani da wanda zan tunkara in sanar da shi halin da nake ciki. Amma abinda ke bani takaici na kasa faɗa masa cewa nasan abinda ya ke aikatawa. Haka son sa a zuciya ta yana nan daram na kasa jin haushin sa, sai ma neman yi masa uzri na ke yi. Ƙila ya fara ne lokacin da yake bashi da mata, yanzu aiki na ne in rabashi sa su. Ko ƙila su ke binshi kuma iyakacin su a waya sai turo hoton kawai. Dan haka na ƙara dagewa na daina bacci sai na jira shi ya dawo kuma duk yadda ya ke so haka nake masa, sannan da safe kafin ya fita wajibi ne sai na sauke wani haƙkin amma da an kwana biyu in na duba wayarsa sai inga anyi masa sabon turi na tsiraici. Gashi na kasa daina dubawa, sai na yanke shawarar komawa ga Allah ya bani mafita. Sai mun kwanta yana bacci zan tashi ina faɗawa Allah halin da nake ciki ya taimake ni ya shirya mijina ya rabashi da wannan muguwar ɗabi'ar. Yau ma ina tsaka da addu'a sai kuka ya ƙwace min ina kuka ina faɗawa Allah cewa. Ya Ubangiji! Kasan halin da na ke ciki Allah kai ka kawo min wannan bawan naka har ƙofar gidan mu Allah ka sani ban taɓa aikata zina ba, Allah na san cewa akwai wani abu da ka ke nufi da wannan haɗin da ka yi. Bani da wata mafita ko wata dabara Allah ka taikeni ka fidda shi a cikin wannan halin. Kuka ya tiƙe ni. Na shafa addu'o'in na ta shi naje gefen shi na kwanta na matsa na shige jikinshi kamar yadda muka saba kwanciya. Sai naji ya matseni tsam ya ce wai "Baby wace damuwa ce da ke wadda duk dare sai kin tashi kin yi wa Allah kuka. Nasani shine wanda ya fi dacewa da ki kai masa kukanki, amma tunda ya baki ni Baby ki faɗa min mana ko zan iya yin wani abu akai in bazan iya yin komai ba sai in taya ki roƙon sa?" Na sake matse shi nace nace wai dama ba bacci ka ke yi ba? Ba wata damuwa ce da ni ba, ina yi wa Allah godiya ne da ya bani kai a matsayin miji wanda wayo na da dabara ta ba su isa su bani ba. Ya sake matseni ya ce "Baby ni ne ya kamata inyi wa Allah godiya samu mace irin ki sai mai babban rabo.Dan haka karki damu ki kwantar da hankalin ki ni baku ne har aljanna." Cikin kwanaki yanayi na ya fara canzawa na rame kuma na rage walwala. Shima ya lura da haka ya matsa min da tambaya na ce ba komai, ya siya min waya Iphone 13 yace in bawa Jamila waccan buɗe min Whatsapp duk wai dan in saki raina, ya min gargaɗi wai kar in shiga wasu groups irin na Whatsapp ɗinnan wanda ake zuga mata, wai Maman Mubina ta taɓa shiga wani group wanda suka yi ta samun matsala da shi. " Nace masa zan kiyaye nace wa Hajita ta taya ni yi masa godiya dama a gaban ta ya bani. Yana ta ƙoƙarin in saki jiki in koma walwala ta amma na kasa. Ina kuma ci gaba da bibiyar shi ta wayarshi ina ganin yadda yake ci gaba da hulɗa da mata, abinda na gama lura shine ya kan haɗu da wasu, wasu kuma baya haɗuwa da su,amma yana ba su kuɗi. Cikin haka azumi ya gabato. Da dare yana falon Hajiya da yake tun daga wannan ranar nike zuwa ina zuba masa abincin dare da na safe, wanda da ashe Azima ke zuba masa na daren na safe kuma da kansa. Daga shi har Hajiya ni ce ke zuba musu. Hajiya tace Baby kin kuwa san Azima bata da lafiya kin duba ta? Nace bansani ba,tace to ya kamata ki yi mata sannu jiya da yau bata je makaranta ba. Nace Subhanallah! Na tashi na nufi duba ta tunda na zuba musu abincin. Tana lullɓe na mata sannu ta amsa,har zan fita sai tace "Ki faɗawa Yaya ina jiran shi." Na yi shiru,sai na juyo nace kamar yaya kina kina jiranshi? Tace " Shi ya sani." Sai na ji gaban ya yi wata muguwar faɗuwa tsoro da fargaba sun kamani kar dai har wannan yarinyar...Ta katseni, "Ko kina nufin baki san ni wacece a gurinsa ba?" Bance ƙala ba na fice domin yin sa'insa da yarinyar zai zama zubda ƙimata. Na koma Falo na samu su Hajiya suna zancan Umara, nace da Hajiya zan jira in shafa maki maganin ƙafa tunda Azima ba lafiya. Tace "To Allah ya yi miki albarka jiya ma ba'a shafa ba. Na koma gefe ina kallo a talabijin. Yace "Hajiya kujeru goma ne a wannan karon an ƙara biyu, yanzu sai ki bada sunayen mutane bakwai ni da ke da kuma Baby mune cikon na goma." Kamar a mafarki na ji maganar, zani Umara, amma sai dai ba dani suke magana ba dan haka sai na share na yi kamar banji ba. Hajiya ta ce ka cire Baby a maganar ta fiya Ummara da aikin Hajji sai wata shekarar. Ban waigo ba kuma ban nuna ina jinsu ba. Ba tare da ya tambayi ba'asi ba ya ce "To an cire ta." Suka ci gaba da lissafin su. Sai kusan goma da rabi tace zo ki shafa min maganin nan. Na zo na fara shafa mata gami da matsa ƙafafun, tace "Kai amma na ji daɗin yadda ki ka matsa min ƙafafun nan, ina ganin ma dai ke zaki koma shafa. min maganin nan domin Azima sai ta koya. Nace to insha Allahu zan ke shafa miki. Shamaki yace, "wai kuwa likita ya duba jikin Azimar ? Hajiya tace ya duba ta,kasan bata rabo da zazzaɓin cizon sauro, can take zuwa ɗan lambu can har magariba. Na dube shi, baka je ka duba ta bane? Yace "Sai na shiga zan kwanta sai in duba ta.' Daya ke ina son in wanke zargi sai na raya cewa zan bi bayanshi. Haka kuwa nayi mun tafi tare mun sallami Hajiya na ce masa bari inje ɗakina in ɗakƙo kayan bacci. Yana shiga falon shi na dawo na shiga falon dai-dai lokacin yana fita ƙofar da zata kai shi gurin su. Na bishi sai da na ga ya tura ɗakin Azimar ya shiga sannan na bishi ciki faduwa gaba tare da fatan kar zargi na ya zama gaskiya. Dai-dai Window bana jin komai na yanke shawarar in afka ɗakin kawai tare da sallama ko zan tsinci kalma guda ɗaya da zan gamsu. Dan haka sai na afka kawai tare da sallama. Yana tsaye bakin gadon ya maida hannuwan shi duka baya, tana kwance riginnine tana kallon shi yana magana. Kalma ɗaya na tsinta a maganar itace.. " Baruwana..." Na kalleshi sai na ga ya yi alamar rashin gaskiya amma sai ya da ke. Na dube ta sannu da jiki Azima fuskarta ba walwala tace Yawwa. Na dube shi, Nace ta ƙi tasha magani ne baji kana cewa baruwanka? Da sauri ya ce ba maganar ki ɓace, muje ya dube ta yace "Allah ya ƙara sauƙi." Na sake kallon ta ƙwalla ce a idanunta,gaba na ya faɗi ko dai ya haiƙewa yarinyar nan ne to Allah ya sa ba ciki ne da ita ba. Sai naji na kasa jan ƙafafuna na tsaya ina kallon ta. Muryar shi ce ta katse ni. "Muje mana Baby" Na ja ƙafa na bishi dai dai window yara ya tsaya yana kallon su. Ni kuma shi nake kallo ina me takaici abinda ya ke aikatawa amma kamannin shi na salihan mutane ba zai taɓa bari a zarge shi ba. Ya yafito ni da hannu na isa gurinsa ya kama kafaɗa ta yace Kalli yaranki suna ta bacci 'yan rigim. Na lalle su abin sha'awa kowacce laf a gadon ta. Nace Ina son yaran nan sosai musamman Anisa ƙila domin ta kasance ita ce ƙara. Yace "Ba domin tana ƙarama bane, tun ranar da mahaifiyar ta ta haifeta kowa ya ganta sai ta shigar masa rai." Nace Allah sarki, wai kuwa iyayen su suna zuwa su gan su? Yace "Gaskiya dai ba sa zuwa,kuma Hajiya ce ta tsara haka,amma duk hutu ana kai su suyi sati ɗaya sai a ɗakko su." Na ɗaga kai sannan nace Allah sarki amma kana yi wa yara nan addu'a ko Allah ya tsare su daga sharrin zamani. Yace "Baby daga dukkan sharri na ke musu addu'ar tsari." Ya kama hannu na muje muje ɗaki ki faɗa min yaushe zaki bani ta wajen ki Baby Zeena ɗin? " Na bishi ina faɗin ni bana son ma in haihu. Bansan a fili na furta kalmar ba sai da naga ya tsaya can. Na kalli fuskar shi launin fuskar shi ta canza gaba ɗaya, wannan ce rana ta farko tunda na zo gidan da naga ɓacin ransa a kaina, ya tsira min ido take fargaba da tsoro suka tsirga min. Ya fincike ni zuwa ɗakin baccin sa ya tura ni kan gado ya jawo kujera ya zauna a gabana ya ce "Maimaita abinda ki ka faɗa." Na girgiza kai cikin tsoro tare da ɗora tafin hannuna a bakina. Yace "Ki maimaita!" Yadda ya yi maganar da ƙarfi sai na tsorata hawaye suka soma zubo wa,nace nifa na yi tsammanin a zuciya na yi maganar. Yace "To me yasa zaki fadi hakan ko a zuciyar ki? Kice ke bakya son ki haihu to faɗa min da lilinki kuma kar ki sake ki min ƙarya." A zuciyata dalilina saboda neman matan da ya ke yi ne, kuma naji ance duk abinda ka yi wa ɗan wani sai anyi wa naka. Amma bani da damar faɗar hakan dan haka sai nace Ni dama na faɗi haka ne saboda ina jin tsoro kada in haihu ni ma ka sake ni kamar yadda ka saki su Maman Anisa kuma ka karɓi 'yar ka kabar ni ina tunanin ku. Na kai ƙarshen maganar da sakin wani kukan. Ya tashi ya dawo bakin gado ya janyo ni jikinsa ya rungume ni tsam. Yace" Baby ni da ke babu abinda zai rabamu sai mutuwa, akan ki na fara soyayya duk auren baya ashe ba soyayya na yi ba sha'awa ce kawai." Na ɗago na dube shi nace dama ana aure saboda sha'awa? Yace "Ni kaina ban gane hakan ba sai bayan auren sai inji duk sun fita a raina." Nace sai kawai ka sake su? Yace 'A'a Baby babu wadda na saka saboda hakan sai bisa wani dalili na Hajiya wanda har yanzu ban san shi ba." Nace Ni ma na fara fita a kan ka ko? Cikin far gaba na yi tambayar. Yace "Baby kullum ƙara son ki nake yi, da kika ce baki son ki haihu kalmar ta min zafi, ya kai hannu ya shafa cikina, na ƙosa inga wannan shafafen cikin ya tasa ya ɗanyi tudu, ina son inga naki salon laulayin dame zai zo." Na zuba mishi idanu a zuciya ta kuwa tunowa ta ke da kalaman da ya ke rubutawa na batsa da hannun sa yana turawa matan banza,ga waccan yarinyar da nake zargin su da ita. Ya hura min ƙwayar idanu tare da faɗin "Kamar kina min kallon tuhuma Baby." Nace Me zaka yi wanda zai sa in tuhume ka? Kai mijina ne mai gaskiya da riƙon amana,ga ibada kyauta da sadaka gidan ku ya yi fice, gashi ka tsare kanka daga sharholiyar zamani ta bin matan banza da yawancin mazaje ke yi,ko tunanin bayansu basa yi,. Ina matuƙar tausayin ahalin mazinata, domin sai uba ya ja a yi wa 'yarsa a banza ba tare da hakkinta ba .Ko miji ya ja wa matar sa ɗa ya jawa uwarsa...Hannu ya sa ya rufe min baki tare da faɗin "Ki taya su addu'a Allah ya shirye su. Ni yaushe ma na samu lokacin matata har bare in tsaya neman wasu matan. Ina da kamar ki wace damuwa gare ni. Baby komai na ke so kina min yadda ki ke sakin jiki da ni a gurin kwanciya ban taɓa samun haka ba. Kina kore duk wata sha'awa tawa. A zuciya ta nace kaji ƙarya. Ko a wannan daren na yi bincike a wayarsa, kuma sunyi alƙawari da wata za su haɗu ranar Lahadi da ƙarfe sha biyu. .... A Cikin kwanaki kullum ina yin tunani aka yadda ya kamata in daƙile wannan haduwar ta sa da karuwar nan, kwata kwata bana son yasan nasan abinda ya ke aikatawa domin ɓoye min ɗin ma alfarma ce, in har namiji ya na aikata wani laifi ya ɓoye miki alfarma ce kar ki sake ki binciko, sannan in har kin gano to karki nuna masa domin zai yi borin kunya ne ya nuna miki bai damu ba, sannan zaman lafiya ya ƙare. Zuciya ta ce ta yi min wannan karatun don haka sai na ƙara yin ƙoƙarin daurewa. Kuma na fahimci cewa kowane iyali suna da tasu matsalar wasu rigingimu da munafirci, kamar ahalin su Abbanmu kenan. Wasu 'yan shaye shaye suke da su a cikin nasu ahalin.Wasu kuma ɓarayi. To sukuma nan manemin mata Allah ya basu gane nima ya zama cikin ƙaddara ta. In na tada bala'i na tafi bansan dawa zan haɗu ba a gaba. Ranar asabar na sake bincika wayar sunyi magana cewa zai aiko a ɗauke ta tsakanin shabiyu zuwa ƙarfe ɗaya. Na tashi zaune na ƙare mishi kallo cikin dare yana bacci nace zan gwada wata dabara Allah ka tsaya min. Na riƙe cikina ina ta juyi ina ɗan kuka ina faɗin wayyo cikina. Ya farka a gigice ya kamani yana tambaya ta, da kyar nace cikina ne ke ciwo. Ya tashi ganin yadda ciwon ke ƙara tsananta ya kira wayar Hajiya ya faɗa mata. Tace "Subhanallah! Ka zo ka amshi ko plagin ka bata kafin asbashi a kira likita." To haka dai aka kwana a kaina ina birgima,yau da ga salla wannan zaman na safe na gurin Hajiya ranar bai samu ba, da zai tafi salla sai na yi laf kamar bacci ya sace ni. Yana fita na tashi na yi salla na dawo na ɗora ina juya juya har na faɗo daga kan gadon. Shi kuma bayan sun gaisa da Hajiya ta tambayi jikina yace sai gefin asbahi sannan bacci ya ɗan sace ni, yace shi kanshi bacci ya ke ji yanzu idanunshi sai raɗaɗi suke yi. Hajiya tace "Ka kira likitan ko?" Yace munyi waya yana hanyar zuwa nan ɗin,. Hajiya tace "Allah ya sawaƙa kuma ba ciki gareta ba ko?" Shamaki yace gaskiya dai bansani ba, amma a wannan sati tayi al'adar ta. Hajiya tace To" bari likitan ya ƙaraso muji." Kiran likitan ya shigo,Shamaki ya ce gashi nan ma bari in shigo da shi. Har Hajiya suka nufin ɗakin Shamaki ni kuwa lokacin ina tsaka da kukan baƙin ciki jin motsin su ya sa na dafe ciki na shiga juyi. Shamaki ne ya rugo da gudu yana faɗin "Subhanallah faɗowa ki kayi haƙa Baby! Ya ɗauke ni ya mayar kan gadon yana min sannu, sai naji muryar Hajiya itama tana min sannu cikin magana da ƙyar nace a kai ni gurin Ummanmu zan mutu ne. Hajiya tace "Inda mutuwar ce 'yannan wane ke ki furta ta,zafin ciwon ne Allah ya baƙi lafiya likita ka duba ta sosai ni bari in koma Allah ya sawaƙa." Duk inda likita ya latsa da hannu a cikina sai in saki ƙara, yace a sani a mota kawai muje Asibiti a yi hoto domin a gano ina matsalar ta ke, ya kira Hajiya ya faɗa mata, sannan ya canza kaya ni kuma ya zira min hijabi akan kayan bacci ya ɗakko ni kamar ya ɗau jinjiri muka fita mota. Iya gwaje gwajen likita bai iya go komai a cikina ba, don haka sai ya gayyaci wani likita wanda ya yi shura a fanni cikin kafin yazo aka min allurai dan rage raɗaɗi sannan aka samin ruwa da allurar saka bacci. Bacci ya yi gaba da ni wanda har likitan ya zo suka yi hoto an gane wane ina da sanyin mara da kuma tsakuwa wanda ake ganin tsakuwar ce ma ta soma taruwa, za a bani maganin ta taru guri guda in ya so sai a yimin aiki. In kuma anga yiwuwar ba sai anyi aiki ba sai a bani magani ta narke. Ni dai ban farka ba tunda a kwai bashin bacci sai kusan ƙarfe biyu, ina ganin Asibiti na tuno komai da komai zan motsa sai ƙaran wayar shi ce ta tashe ni, bai san na farka ba yana magana can ƙasa ƙasa daga can kusa da bakin ƙofa da yake kunne na kamar na maciji ya ke ba dai jiyo magana ba, naji yana faɗin. "Na faɗa miki cewa na miki magana ta Whatsapp ki duba mana mata ta bata da lafiya yanzu haka muna Asibiti in na samu lokaci za mu sake saka rana don haka karki sake kiran wayata. Alhamdulillah na furta a hankali, na wahala kuma na yi ƙarya,amma na yi nasarar hana aikata babban laifi wato zina. Ya dawo ina miƙa tare da salati, yace "Baby kin farka sannu ya jikin.?" Ya kama hannu na yana murzawa. Na zuba mishi idanu, kishi da son shi suka sake tirniƙe ni. Nima na matsa hannun shi a hankali nace dan Allah kana so na sosai? Ya tsuguno ya ɗora karan hanci shi a kan nawa, yace "Baby me yasa ki ke ta kokwanto?" Ka sake tabbatar min, na faɗa hawaye suna zubowa daga cikin idanuna. Yace "Baby ina matuƙar son ki." Na sa tafin hannuwa na guda biyu na ɗora akan kumatunsa, nace Ni kuma nayi maka alƙawarin zan yi maka duk wata biyayya zan rufa maka duk wani asiri zan baka duk wata kariya wadda nake da iko. Ya ɗanyi shiru, can ya yi murmushi "Baby za dai ki min biyayya amma rufin asiri ko kariya ai nine zan miki wannan amma ki taya ni da addu'ao nan da ki ka saba." Nace to ba damuwa muje gida tunda na samu sauƙi, gashi baka je kasuwa ba kai sam yau. Yace "Ya zanje kasuwa mata ta tana cikin mawuyacin hali." Nace na gode da kulawa. Yace bari inje in yiwa likitan magana. An sallame ni da tarin magunguna,muna isa gida Hajiya ta min sannu su Juma kuwa har ɗaki. Ranar dai Shamaki bai fita kasuwa ba,kuma banga Hajiya ta damu da rashin fitarsa ba, yana gurinta kaɗan kaɗan ya zo ya duba ni. Kwana uku bayan wannan diramar ina zaune gaban Hajiya ina yi mata tausa a ƙafa, tace "Me yasa baki sanar da iyayenki rashin lafiyar ki ba? Irin wannan ciwo da ki ka yi mai azaba zai iya kai mutum lahira." nace na ga ana kula dani sosai kuma kar in tada musu hankali shiyasa. Tace "Kinyi tunani mai kyau, Allah ya ƙara lafiya, ta ci gaba Shamaki ya na sonki, ki yi amfani da hakan ki taimaki rayuwarsa." Kalaman suka ɗaure min kai, me hakan ke nufi? Na tambayi zuciya ta. Hajiya ce kawai zata iya wayar min da kai, don haka sai na ce. Tayaya zan iya amfani da haka in taimake shi? Kuma wane irin taimako? Tace "Babu buƙatar dogon bayani ni dai zan ci gaba da kula da yiwuwar hakan." Nace to Allah ya bani iko, ni zanyi koma menene matsawar hakan zai taimake shi. Hajiya tace kin kyauta Juma ta shigo ta zauna tace ina son magana da ke ne Hajiya. A duk lokacin da Juma ta yi irin wannan furucin Hajiya ta san tana buƙatar su keɓe ne. Dan haka sai ta ce, " Rabi'atu ba mu guri mu yi magana. Na tashi na nufi gurin yara. Azima tana zaune kamar kullum da littafin a hannun ta. Ban damu da ƙin amsa sallama ta ba,domin nasani ta saba. Yaran suka nufo ni su duka suna tambaya ko zanyi musu tatsuniya. Nace su bari sai gobe Alhamis tunda babu islamiyya in mun gama karatu sai in yi musu. Juma tayi sallama muka amsa tace "Azima Hajiya tana kira." Sai da ta ja dogon tsaki sannan tace faɗa mata ina zuwa. Juma ta jima da tafiya kafin Azima ta sake yin tsaki ta yashi tana ƙunƙunai. Nabi bayanta da kallo ina mamakin wani faɗi da naga ta yi. Ji nayi duk na tsargu, na tashi na nufi ɗakina, Gaban hoton mu na tsaya wanda yake bani kyauta ina kallo shi. wayata ta yi ringin na ɗauka na kalli fuskar wayar na sa a kunne tare da faɗin babban baƙo ka dawo ne? Yace "Duk jan lokacin da aka yi ana nema min suna ƙarshe in ƙare da wani babban baƙo babu ko daɗin ji." Na yi dariya nace in har kaine Babban baƙon mu na ranar saukar karatunmu to kuwa sunan da zaka ci gaba da amsawa ke nan. Yace "A hakan ma ni ne da godiya, domin a keɓaɓɓen lokaci akan kira ni da Baby sweet heart da sauran sunaye cikin shagwaɓa. To kina ina ne yanzu?" Nace ina zani ina gida akwai wani abu ne?" Yace "a'a' Na kira Hajiya ne bata ɗaga ba, nace ina ɗakina ne amma bari in duba maka, kariƙe wayar har inja falon, yace "to kije ina jinki. Na isa falon Azima ce zaune su da Hajiya kan Azima a ƙasa kamar dai tana kuka, Hajiya kuma cikin wani yanayi da bazan iya fassarawa ba. Na ƙarasa nace Hajiya Shamaki ne ya ke son ku yi magana. Hannu kawai ta ɗaga min, wanda bana bukatar sai an faɗamin cewa bata son jin maganar kowa. 🖊️🖊️🖊️ *HAMSHAƘIYAR UWA🧕🏻* *NA* *HALIMA ABDULLAHI K/ MASHI* _PAID BOOK_ _Kuɗin karatu ₦600_ _Account number 0700549935 Halima Abdullahi Access Bank a turo shaidar biya ta wannan number 08140004302 ko katin Mtn_ _Phone 08140004302_ *DOKA* _Ban amince wani ya ɗora littafin nan a wani Social media ba,ko a maida mini shi Audio ba tare da iznina ba yin haka daidai yake da fuskantar fushin hukuma. A kiyaye_ *Masu son a Tallata masu hajarsu suyi magana ta wannan number 09068032427* *Page 34* Ta katse ni, "Bakya buƙatar dogon tunani Rabi'atu, akwai wani sirri ne da ki ke ɓoye wa na sa?" Na girgiza kai babu Hajiya. Tace "Gaskiya ban yarda ba, kina dai rufawa mijin ki asiri ne, ina son ki sani kalmar ki da kika furta ita take nuna cewa mijinki ya na leƙe leƙe." Na ce Subhanallah Hajiya bana zargin sa kuma bashi da kama da haka, in kin duba sam bashi da lokacin kansa bare na yawon banza,kawai dai na furta ne saboda akwai masu yi, ni kuma godiya ce ga Allah da bai bani irin wancan ba,ya bani wanda zai aje mu mu huɗu. Hajiya tace "To iya magana Sarkin zance Allah ya shiryar da duk ɗan musulmi. Nace Ameen,tace tashi ki kai masa kankanar, saura kije ki faɗa masa abinda na ce game da ƙara aurensa. Na ce bazan ce komai ba. Na tafi da kankana na tura falon a hankali na shiga baya fakon na aje masa a gurin da yake ajewa na nufi ɗakin zan shiga da yake tun da na saka shi a tarkon zargina bana yin wani kwakwaran motsi in zan shiga gurinsa. Cikin Sa'a naji yana waya, yana faɗin "Sweetheart gaskiya ban taɓa samu mace mai suna mace kamar ki ba, a tafiyar nan ta sati ɗaya kin ji dadi banso muka rabu ba. Ta faɗa masa wani abu sai naji ya ce "Da gaske Babyna to ai kin haɗu ne, bana son a yi min kishiya don Allah a dai riƙe min amana. Kuma a turo min hotuna in kalli abubuwan... Hannu na saka na toshe kunnuwa na,sannan na juya da sauri, cikin rashi sa'a na bigi wata tukunyar fulawa da ke aje a gefe sai ta faɗi. Da sauri ya katse wayar ya fito,daidai lokacin na murɗa ƙofar zan fita, yace Baby! Yadda ya kira ni kasan cikin fargaba ya ke. Bazan iya juyowa in Kalle shi ba,kalaman sa suna min yawo a cikin kai dan haka sai kawai na fice,da gudu na ƙarasa ɗakina kan gado na faɗa ina maida numfashi na soma karanta duk wata addu'a da ta zo baki na. Ina jin ƙarar buɗe ƙofa nasan shine, don haka sai na soma ƙokarin daidaita yanayi na. Ya shigo ya tsaya yana kallo na. Na ɗago da kyar na zuba mishi ido. Hawaye suka soma kwaranya a idanuna. Ya zauna jiki a sanyaye, ya ce. "Menene ki ka fita da sauri ina kiran ki?" Cikin rawar murya da zubar hawaye nace babu komai. Ya kama hannuwa na, a yau sai naji tafin hannun sa mai taushi kamar ƙaya . Yace Baby dole akwai wani abu ki faɗa min. Na girgiza kai ba komai. Na saɓule hannu na daga nasa,kaje ka ci kankanar ka na ajiye. Ya ƙara kama hannu na "To tashi muje mu sha sai mu kwanta. " Na sunkuyar da kai, ka yi haƙuri yau zan kwana a nan. Ya yi shiru, yana ƙoƙarin tabbatar da zargin sa,tabbas yarinyar nan ta ji wayar sa. Ya sunkuyar da kai yana tunanin abinda ya kamata ya yi. Na zame a hankali na kwanta ina nanata ambaton sunaye Allah a zuciyata ba shakka duk matar da mijinta ke neman matan waje alal haƙiƙa tana cikin masifa.Na lumshe ido hawaye suna kwaranya ta gefe. Ina jinsa ya miƙe jiki ba ƙarfi ya kama hanya,na bishi da kallo har ya fice ya rufo min ƙofa,na tashi na zauna zaman dirshan na saka kuka. Nayi mai isata, sannan na miƙe na shiga ban ɗaki na ɗauro Alwala na zo na shiga jero salla, ba zan iya ƙirga yawan sallamar da na yi ba har sai da naji ina jin kiri sannan na zube a sujjada ina raira kuka a gaban Ubangiji na kasa furta komai sai faɗi nake Ya Allah! kai ne mahalicci na, Allah ka gani,Ya Allah! Ka gani. Bacci ya ɗauke ni a nan, a durƙushe. Kiran sallar farko ya farkar da ni, na tashi duk jikina ya yi tsami saboda irin kwanciyar da nayi dakyar na yo alwala nazo na ɗora sallah. Aka tayar da sallah inajin yana ƙwanƙwasa ƙofa ta,ban tashi ba na ci gaba da sallah. Bayan na idar na zauna ina tunanin kishin me zan tsaya yi da duk wadda zai auro, domin da ya kawo su ya aje zai komawa matan waje, kuma duk yadda aka yi Hajiya tasan yana bin mata, tana zaton ko na gano ne. Yanzu wane mataki ya kamata in ɗauka shine damuwa ta. Na farko bazan nemi ya sake ni ba, domin yin hakan babban laifi ne,banda haka sonshi ko kyas bai ragu a zuciyata ba amma na san tabbas ina jin haushin sa a yanzu,yana faɗawa wata ƙaruwa wai shi bai taɓa jin mace irinta ba,ni kuma fa? Wata zuciyar tace ki dafa shi da ruwan sanyi dan kina sonshi kar ki yarda ki zama kamar wata shashasha. A fili nace Allah ka bani basirar yadda zan tafiyar da wannan bawan naka.Allah ka shiryar da shi. Wayata ta soma ringin a firgice na ɗakko ta kardai wani abu ne ya faru a gidan mu. Ashe shine, yace ki zo ki same ni a gurin Hajiya. Nace to. Ashe shima haka ya kwana cikin tashin hankali ya tabbatar taji maganar dan haka sai da ya gama tunanin abinda ya kamata ya yi ƙarshe ya yanke shawarar kawai ya faɗawa Hajiya ko ma dai menene ta shawo kanta domin shi duk nauyin ta ya kamashi balle da ya zauna yana tuna kalaman batsa da suka dinga musaya da yarinyar bai san tun yaushe ta shigo ba. Inhar ta ji komai gaskiya ya yi abin kunya babba. Na durƙusa na gaida Hajiya kamar yadda na saba. Na dube shi shima na gaishe shi kamar ba komai. Ya kalli Hajiya ya sunkuyar da kai, sannan yace Hajiya na kawo kaina ne bisa ga wani laifi da nayi Wa Baby,ina son a taya ni bata haƙuri kuma insha Allahu zan kiyaye. Ciki mamaki Hajiya ta ke kallon baƙon lamari Shamaki yana neman afwar Babu har da haɗawa da ita,to wane irin laifi ne haka? Na katse mata tunani da cewa Ya Salam! ni ce kaimin laifi? Yace ki bar wani alaye Baby na yi kawai tun jiya kin dage ba komai,amma kina ta kuka shi kuka dama ana yin shi haka kawai ne, kuma na ga tsanata a ƙwayar idanunki kin ƙauracewa shimfiɗa ta ko bacci banyi ba. Bazan jure kiyi fushi da ni ba. Na kalli Hajiya wadda ta tsura min ido, na sunkuyar da kai. Hajiya tace ka tashi ka shiga ciki ka bamu guri. Na gyara zama,ta ce Rabi'atu jiya ya muka yi dake anan gurin? Na ɗago na dubeta ina ƙoƙarin tunawa, nace munyi magana da yawa musamman ta aurensa da Azima. Tace "Yawwa amma ya muka rabu?" Nace kince kar in nuna masa munyi maganar. Tace Yawwa to kuma ya akayi kika yanke masa irin wannan hukuncin na azabtarwa?" Nace Hajiya wallahi yadda muka yi maganar nan a nan gurin wallahi a nan nabarta. Bance banji zafin kishi ba,amma wannan ba laifi bane dan zai ƙara aure zan bashi duk wani goyon baya Hajiya wallahi bazan ɗaga masa hankali ba. Tace to faɗa min menene ya yi miki?" Na sunkuyar da kai nace Hajiya kiyi hakuri nasan Shamaki ɗanki ne,kuma kina sonshi fiye da kowa, amma ni kuma mijina ne akwai wani sirri tsakaninmu wanda ya kamata in suturta shi daga ni sai shi sai Allah. Ina neman alfarma ki bar wannan maganar ta wuce a gurina ki ƙara yi masa addu'a kawai. Yau ce rana ta farko da naga jikin Hajiya ya yi sanyi harma ta rasa abin faɗi na kusan sakwan talatin. Sannan ta ja wani dogon numfashi tace, "Ki sani riƙe abu a zuciya yana haifar da ciwo,tattauna Matsala da wani yana rage damuwar kuma ni ce mafi dacewa ki tattauna wannan damuwar da ni." Nace Hajiya dole ne mu koyi yadda zamu kashe mu rufe domin samun kwanciyar hankalin ki, duk da ban kasance likita ba, a shekarun ki yanzu bakya buƙatar duk wani abu da zai tada miki hankali. Tace "Babban abinda ya fi komai ɗaga min hankali shine inga Shamaki a damuwa, ina yin kowane irin abu dan in samar masa da kwanciyar hankali aurenki misali ne." Na yi shiru, ina tunani Hajiya tana yi wa ɗanta makauniyar soyayya wadda ta sa sam bata iya hango matsala. Na dube ta, zan yi iya yi na inga bai shiga cikin wata damuwa ba daga yau. Naɗaga yatsa kamar mai ɗaukar alƙawari. Bata ce ƙala ba ta ɗaga waya ta kirashi,ya zo ya zauna yana satar kallo na. Tace "Shamaki matar ka ta dage akan babu komai da ka yi mata, sai dai ina mai baka shawara ka yi ƙoƙari ka gyara abinda ka ɓata a idanunta. Ya kalle ni, na yi ɗan murmushi ka yi hakuri da yanayin da na saka ka a ciki. Shi dai idanu ya zuba min yana kallona. Anisa ta shigo ta nufi gurin Hajiya da littafi a hannu ta gaisheta sannan ta gaida Dadynsu,sai ta dube ni Momy ina kwana, ta zauna kan cinya ta,tace Momy Anty Azima bata yi min Homework ba. Na amshi littafin ina dubawa, nace to zo muje gefe mu yi. Na koya mata Rahin ta zo ta tafi da ita domin yi mata shirin makaranta. Na dubi Hajiya suna magana ƙasa ƙasa da Shamaki nace zan dawo kafin su Juma su haɗa abin karyawa. Lokacin da ya shigo domin shirin tafiya kasuwa ina gyaran gadon shi, ya tsaya ya harɗe hannayen shi yana kallo na, na ce akwai wani abu ne? Ya girgiza kai sannan ya shige banɗaki. Na fito masa da kaya kamar yadda na saba ya shirya tsaf na ɗauki jakarsa na rataya a kafaɗa. Ya janyo ni zuwa jikinsa ya rungume ya sa hannuwan shi guda biyu ya ɗago fuskata ido cikin ido muke kallon juna, yace "Baby yanzu bazaki faɗa min.. Nasa tafin hannu na narufe mishi baki tare da faɗin shissss ya wuce babban baƙo. Muje ka tafi Allah ya tsare gabanka da bayan ka. Yace kimin alƙawarin cewa bazaki yi kuka ba." Nace bazan yi ba. Ya sunbaci goshina sannan muka tafi tare. Cikin satin na zama cikin taka tsantsan kuma na duba wayar shi naga 'yan mata sun masa magana amma duk bai bada amsa ba. Babu daɗin ganin haka tabbas an ɗan samu ci gaba domin hakan da ma ya taimaka inda na tada bala'i da sai ya tada borin kunya ya yi bala'i kuma ya murje harma ya ke min gadara a gabana sai ya yi wayar shi tunda ya lura bazan iya komai ba. Matar Abokin shi Alhaji Shamsu ta haihu , yace in shirya da dare zamuje barka. A gaban Hajiya ya yi maganar na ji daɗi domin ina son muna ɗan fita da shi. Hajiya tace ka je kai kaɗai ita kuma anjima ta shirya direba ya kaita ka bata abin barka. In kuma taron suna zata je shikenan sai ta bari sai ranar. Ya kalle ni kamar yana son yaga yadda zanyi tunda yasan ina son mu fita da shi na sha faɗa masa cewa ina son mu ɗan fita ko a ƙafa ne, sai ya ce inyi hakuri in ya samu lokaci ƙasar waje ma zamu fita. Washe gari ya bani zannuwa biyu da dubu goma ya ce inje barka shi baya son zuwa suna ɗin nan. Nace to. Na sanar da Hajiya tace to in shirya baya azahar. Mace mai fara'a maman Haidar wai takwara aka yi wa Shamaki, nace a lallai ki ce ni aka yi wa haihuwar amma bai faɗa min ba. Tace ai bai faɗa masa ba sai ranar zaiji. Nace to ki ce in zuge baki na. Tace gaskiya kam. Da tare zamu zo sai kuma yana da uzri. Tace "Ko kuma Hajiya ta hana ba." Nace Ya zata hana mu fita tare, cikin mamakin yadda aka yi ta san maganar na yi tambayar. Tace "Ba gulma ba amma ko zuwanki na sha mamaki, duk matan Shamaki sai dai su saci hanya su ziyarci mutane, bata son su yi hulɗa da kowa, shiyasa ki ka ga ko gurinki ban zo ba." Na gyara zama domin jin kanun labarai. Nace to ko domin ni ban jima bane shiyasa bata fara min ba? Tace "Ƙila dai ɗan ke yarinya ce ƙarama shiyasa bakya ganewa. Shekara ɗaya na cika ta ke sa shi ya saki mace tace wai bata ci jarabawa ba,ko uban me ta ke jarabtawa oho mata." Nace ce duk bansan wannan ba,ke ya 'aka yi kika sani? Tace "Tsoro na ke kar magana ta fito." Nace sai dai in ke ki ka faɗa amma ni bana haka kamar kin haƙa rami kin saka. Tace "Ai Kinsan Maman Anisa ƙawata ce munyi makaranta a gurin bikina suka haɗu da Shamaki suka yi aure, kar ki ga irin son da suke yi wa juna amma shekara na cika ta sa ya sake ta. Har yanzu suna son juna kuma tace min kuma zasu iya maida auren su." Gabana ya faɗi amma sai na saki murmushi nace ya faɗa min ai baya ɓoye min komai, ta ce "Haba dai." Nace ƙwarai kuwa. Tace Kenan har irin zaman su da maman Mubina da Meema?" Nace kina shakka ne? Tace "A 'a Naga ita Maman Anisa bai taɓa faɗa mata komai game da su ba." Nace Kinsan so kala kala ne ni komai na shi na sani. Tace ni Uwar gidana sun saba da Maman Meema sun zama ƙawaye tunda matan abokai ne,to ita ke ba uwargidana labarin zaman su shine ta ke bani." Nace dama ku biyu ne? Tace e uwargidana anjima nan zaki ganta tunda muna zama lafiya. " Nace yafi muku sauƙi yaushe zaka tsaya fitina akan namiji? Tace ashe kin gane ga mazan nan namu masu neman matan tsiya kuna nan kuna faɗa wasu na can na faranta musu. Na ce ai kuwa Allah dai ya shirye su. Ta sake kallo na da taji bance komai ba. "Ashe kinsan suna neman mata?" Nayi "yar dariya akwai wani da zaka sheda ne yanzu a maza? Ta taɓa baki tace babu. Amma ya faɗa miki har yanzu suna fita da maman Anisa?" Na yi shiru da alamu matar nan so take ta hasala ni kuma kamar aike. Nace duk na sani, nifa da kika ganni duk wadda ta zubda kanta ta bashi ya bi ya tsallake ruwanta. Ta buɗe baki cikin mamaki, tace "Kin ɗaure mishi gindi kenan? Nace To Maman Haidar ina son mijina ya yi abinda ya ke so. Tace "Yanzu na gane abinda ya sa Hajiya bata nuna muku mugun halinta ba. Ita ke ɗaure mishi gindi yake bin mata." Nace To shi Mijinki wa ya ɗaure mishi nashi gindin? Ta saki dariya gaskiya kullum muna ƙorafi muna masa addu'a. Nace to ya bari? Tace ya dai rage da har a gabanmu yake waya da 'yan matan shi, sai da muka tada balli. Shine yake yi a ɗakin shi . Sallamar wasu mata muka ji ta amsa ta leƙo sai naji tana faɗin a kamar haɗin baki ga Maman Anisa da Maman Meema. Gabana ya yanke ya yi wata muguwar faɗuwa. 🖊️🖊️🖊 ️Na dake domin na gane duk yadda aka yi kiran su ta yi a waya,ko ta tura musu message tun da na lura wayar ta tana hannun ta tunda na zo, amma dai banga ta yi waya ba. Muka bi juna da kallo ni da su, lokacin da suka zauna, na gane Naman Anisa domin suna da kamanni, na kalli. Wadda nake zaton ita ce uwargidan maijego ta ce "Amarsu ce aka zo mana Barka?" Na bi ta da kallo ban amsa ba. Wadda na ke zaton Maman Meema ce tace "Amaryar ma?" Wai a zuwan bata sani ba. Mai jego ta amshe da sauri ta ce "Amaryar Shamaki mana." Maman Anisa ta zaro ido, Tare Da faɗin Shamak dai "Dama ke ce Amaryar Allah sarki, har kin bani tausayi ta yatsina baki, gata yarinya wannan tafi sha biyar ma, kai Allah sarki ya zaman ɗaki? Har yanzu kwanciya bata gundire ki ba.? Kin lura dai gidan Zeena akwai na'ura ki bi a hankali. Ta ci gaba. "Yawwa ki lura da su Juma 'yan leƙen asirin Hajiya ne. Kin gane ai?" Murmushi na yi, Kasu dai kamar wayayyu kuma dai kyawawa ne dan na yarda sun fini a kyau,amma abin takaici babu iji ba iya magana bare tauna kalma. Na maida kallo na ga Maman Meema wadda take faɗin "Ko bata iya magana ne?" Na yi ɗan murmushi sannan nace ina yininku?" "Ai ashe bamu gaisa ba." Inji Naman Anisa. Sai kuma suka amsa lafiya lau." Maman Anisa sai yatsina take yi tana hare harare ta miƙe tana danna waya,can ta kara a kunne sai tana faɗin Dadyn Anisa wannan karon kuma a haka aka ƙare? Duk mu ukun da ka rabu damu muna da kyau da diri bana kuma muciya da zani aka ɗakko." Mai jego ta tashi da sauri hankaɗa ta ciki tana faɗin shiga kiyi a ciki uwar neman jaraba. Na yi ɗan murmushi, ko kusa ban ji wani haushi ba,domin dai ko ma me zata faɗa yanzu dai ni ke da miji to wane kula su zanyi? Maman Meema tace "Nima dai sai kallon ta nake ina mamaki wai ace kamar Shamaki ya auri wannan yarinyar, koda yake tausayi ma ni take bani wallahi, watan ta nawa yanzu?" Kishiyar maijego tace ƙila zata yi wata biyu ko uku. Ta kalle ni " Ki fara ƙirga lokacin barinki gidan. Allah ya sa dai kema kina da ciki, duk rintsi randa gado ya taso dole sai kin shigo ciki." Hajiya dai baƙin ciki take yi kar a zauna da ɗanta a samu gado, da ace zai yiwu ta bawa ɗanta abinda matan shi zasu bashi wallahi bazata taɓa barin shi ya yi aure ba. Na lalle ta nace, da farko banyi niyyar cewa komai ba, domin bani da magana da ku duk kun girme ni, kuma banga laifin ku a cin zarafin da kuka yi min ba, laifi nane da nazo barka har maijego ta kira ku domin ku taru ku ci zarafi na, da sirika ta da kuma mijina. Na miƙe tsaye na turawa mai jegon ledar gashi nan Allah ya raya. Na ciro waya ta na soma kiran layin Hajiya. Ta ɗaga nace Hajiya barka da yamma tace "Yawwa Rabi'atu." Nace direban ya taho ne? Tace yanzu ya kawo min saƙo da nace ya bari sai ya yi la'asar sai ya zo ya ɗakko ki. " Nace in babu damuwa ya zo kawai yanzu. tace to bari insa a sanar da shi. Ina kashe wayar mai jego tana riƙe hannu na haba amarya wallahi ban yi dan in wulaƙanta ki ba, kuma ba wadda na kira kawai dai arashi aka samu. Dan Allah ki zauna mana kafin direban ya zo." Na kwace hannu na nace zan jira shi a waje. Tace "Ki rufa min asiri. Kishiyar ta kuwa sai dariya ta ke yi. Sai kira ya shigo, na duba naga Shamaki ne a zuciya ta nace sun gama waya da Naman Anisa ta gama ci min zarafi na shine ni kuma zai kira ni me zai faɗa min. Amma sai na ɗaga inji me zai ce,. Sai naji yace "Shugabar ɗalibai kina gidan jegon ko kin koma gida?" Wani lokacin yakan faɗa min haka tun da na sa mishi babban baƙo. Take na gane cewa wayar ƙarya ta yi. Nace babban baƙo gani yanzu zan wuce, danma tsofaffin matanka sun zo ana ta labari. Yace "Su waye suka zo!? Nace kaji ni fa. Cikin shagwaɓa na yi maganar. Sai naji ya kashe wayar. Maman Meema tace "Lallai yarinya mune tsaffin?" Kishiyar maijego tace ita ma kwana nawa ne wai maye ya yi amarya. Maman Anisa ta fito ta na fadin wai me take cewa! Ƙaran wayar maijego ya tsai da ita, mijin maijego ne ya kira ta. Ban san me yake faɗa ba, naji dai tana faɗin nifa ba wanda na kira, to ance maka za 'ayi faɗa ne." Sai ga Shamaki ya sake kirana,"Ina fata dai ba wadda ta zage ki?" Nace , To ko an zage ni babban baƙo ai na kai ne. Zan jira direba a waje ko ka yarda in hau adaidaita sahu? Yace "Na yarda ki ɗauki drop ki bar gidan." Nace yanzu insha Allahu. Ina kashe wayar naga duk suna kallo na. Mama Meema tace Abin tausayi kya gama kicifin ki fice ki bar gidan ba dai Hajiya Zeena da Shamaki ba." Na yi mata kallo sama da ƙasa sannan nace, in banci Jarabawa ba ke nan, kinsan wani abu? Ko a makaranta ban taɓa faɗuwa Jarabawa ba,bare ta gidan Hajiya Zeena mai sauƙi, ku rungumi ƙaddara a kwai zafi ka kasa cin Jarabawa musamman ta shiga ajin gaba. Na Kalli Maman Anisa nace daƙiƙi shine ya ke maimaita aji, Allah ya sa dai kin fahimta. Na dubi maijego nace Dole Hajiya ta hana zuwa gidan ire Iran naki domin hakan yafi alkhairi. Allah ya raya miki ɗanki. Na rataya jakata na fice, ina ji suna banza a banza kawai. Ina fita direba yana isowa na shiga muka wuce. Hajiya ta tambayi maijego da jariri na ce duk suna lafiya. Tace "Amma lafiya lokacin da kika kira ɗazu nake jin 'yan surutai?" Nace hira ce 'yan barka ke yi ni surutun nema ya ishe ni shiyasa nace zan tafi. Ta yi murmushi "Mata ai in sun taru basu da labari sai gulma ko hirar mazajen su, mai tunani kuwa bata da wannan lokacin." Nace Allah ya kyauta na shige ɗakina. Da dare Shamaki suna cin abinci, ina dama masa wata fura da ya zo da ita, yace "Wai kuwa Hajiya yarinyar nan ta faɗa miki matan nan sunje gidan Shamsu?" Tace waɗanne matan ne? Yace "Su Naman Anisa da Maman Meema ne nasan tabbas su ne domin Maman Mubina na san bata ƙasar nan, ko tana nan ma bazata zo ba." Hajiya ta Kalle ni, haka ne? Nace e sune, suma sunzo barka ne. Tace sunzo gulma dai,Allah ya sa dai ba su yi miki wata maganar banzar ba." Nace 'a'a hirar su suke yi. Yace "Ba wata hirar su, yarinyar nan bazata faɗa bane Allah ka ɗai ya san abinda su ka yi mata." Na kalli Hajiya wadda ta zuba min ido. Nace To yanzu kam koma menene ai ya wuce, ni nayi musu uzri domin babu daɗi kana son abu ka rasa shi, sannan ka ganshi a hannu wani kuma wanda ka ke ganin bai kai ya samu ba,kuma ace ya zama nasa,kai kuma shari'a ta shata maka layi da shi. Ni na yafe musu, kuma don Allah ku yafe musu ko domin albarkacin 'yan yaransu. Suka kalli juna yace "Kinji ko Hajiya, yarinyar nan a kwai ta da ƙume abu a zuciya, to kafin mu yafe sai ki faɗa mana abinda suka ce." Hajiya ta ɗaga masa hannu, sannan ta ce an yafe musu, Allah ya yi miki albarka. Na soma tunani cewa ƙarya ne baya nema da Naman Anisa, domin na bincike wayar shi babu alamun sunan ta duk da cewa akwai lambobin da ya ajiye su da haruffa. Kwanaki uku bayan wannan badaƙalar sai Hajiya ta aiko Juma musamman ta kira ni, na zo,tace min "Abinda ya sa ta kirani,tana son ne ta min wani taimako ta min gata, amma tasan cewa bazan faɗawa Shamaki ba." nace To, tace "Nasan kina samun komai a gidan nan tafannin ci da sha haka ne?" Nace haka ne. Tace "Amma baki da kuɗi ko taro mijinki baya baki ko sisi ko yana baki?" Nace baya bani. Tace "To zan saka dire ba zai kai ki gidan wani malami zan biya shi zai miji aiki yadda zaki samu damar karbar wani abu a gurin shi." Na ɗago kai cikin mamaki na kalli Hajiya. Tace kina mamaki ne ko?" Babu abin mamaki ina son ya zama sai yadda ki ka ce masa zai yi, kuma zaki nesan ta shi da waɗan can mata.Ina jin takaici iyayenki ya kasa yi musu wata kyauta a matsayin shi na ɗan Alhaji Baita." Ina son ya sai miki mota ki ke hawa da kanki." Yanzu dai je ki shirya." Na tsurawa yatsun kafa ta ido ina kallo,nazarin maganar Hajiya nake yi, kamar ba ita ba mai mugun son ɗanta da ɓoye laifin shi ita ce zata ce wai in mallake shi kuma ita zata biya. Bana zaton za a samu wata uwa ko da mahaukaciya ce da za ta aikata hakan. Wata zuciyar ta ce ko kuma duk cikin gwajin ne. Hajiya ta katse ni. Ki tashi ba'a.bori da sanyin jiki. Na sunkuyar da kai nace Hajiya ki yi haƙuri, ba sai mun yi masa haka ba, bani da bukatar kuɗi a hannu na, domin yana yin komai yadda ya kamata,rannan cewa ki kayi ya bani abin barka na gidan abokinsa kuma ya bani na kai. Iyaye na kuwa aure suka turo ni suka faɗa min cewa ibada ce zan yi har ma suka tabbatar min anan zan samu aljanna baza su yafe min ba in har suka ji layin da na koma. Kuma Hajiya yana yi miki biyayya ni kuma yana sona, don Allah kar mu yi masa komai ba zan iya cutar da shiba. Harara ta jeho min, sannan tace Kin Fini sanin abinda ya dace ne?" Nace a a,tace to duk ranar da na saka lokaci dole kije ayi masa wannan aikin." Na ɓata rai ban kuma magana ba. Tace ni kike ɓatawa rai dan zan taimake ki da dangin ki." Tashi ki bani guri. Na miƙe na tafi ina mamaki. Wai Hajiyar da na sani ce kuwa,kai abinnan fa da ban tsoro. Sam ban faɗawa shamaki ba,sai dai Hajiya na ɗan ja jiki da zuwa gurinta isai in yana gurin, duk da cewa bata sake yi min maganar ba. Umman mu ta sanar da ni tana son ta zo ranar lahadi domin ta ga ɗakina tunda bata taɓa zuwa ba, nace Allah ya kai mu. Da dare ina yi wa Hajiya tausa suna hira da Shamaki nace Yawwa Hajiya Ummana tace zata zo ranar lahadi ta ziyar ce mu. Ta ɗago ta dube ni "Wace ce Ummarki?" Yau ne naji na fara jin haushin Hajiya domin zan jure ni amin komai amma bazan jure a ci zarafin iyayena ba. Shamaki yace mahaifiyar su mana. Ta kalle shi "Ta sanar da kai kenan?" Yace nasan dai ita ce Umman su.. Na kasa ɗago kai dan haushi. Yace Allah ya kaimu amma dai harda su Jamila zata zo ko?" Ya tambaye ni,kamar yana son ya gane ko raina ya ɓaci ne ko kuma ya san cewa ba ayi min adalci ba. Hajiya tace "Yaushe ki ka ce ma?" Na dube ta cikin murmushi takaici nace Hajiya ka wai zance ta barshi ba sai ta zo ba in zuwan nata akwai wata damuwa ne, ni sai in saka lokaci inje ta ganni. Hajiya tace "Tace yi 'yar dariya tare da faɗin yau dai na ga hassala a fuskar ki Rabi'atu ba yadda za a yi mahaifiyar ki baza ta zo gidan ki ba, domin gidanki ai nata ne. Sai ki faɗi abinda ya kamata a bata in zata tafi." Nace ba sai an bata komai ba Hajiya, ita kawai zata ziyarce mu ne. A ɗaki Shamaki yace ki yi hakuri banji daɗin yadda Hajiya ta yi ba." Nace haba ya wuce ka wai. "Yace ki tuna min ana gobe zata zo,nace nan da kwana uku ne zan tuna maka. Yace "Ina ta son mu yi wata magana kuma ina ta tunanin ta ina zan ɓullo wa lamarin ne.." Nace ka faɗa min mana. Yace kin san maganar Azima?" Nace wace maganar a ciki ta auren ku, ko ta ɓarin da ta yi? Ya zaro idanun cikin rawar baki ya ke tambayar "Waya faɗa miki?" Na kama tafin hannun shi na sarƙafe cikin nawa nace nifa 'yar gidan nan ce karka manta, dole zan sani, amma ka sani wajibi ne in rufe duk wani sirri na gidan aurena, wannan amana ce. Yace "Amma me kika sani game da ɓarin da ta yi?" Nace bansan komai ba banda ɓarin. Yace "An saka auren mu wata huɗu ina fatan baza ki shiga damuwa ba." Yawun baki na ya tsaya cak. Gaban sai wani irin duka ya ke yi. Na saɓule hannu na daga na shi, nace a haba ba wata damuwa Allah ya baku zama lafiya, amma dai ita ma a gidan nan zata zauna? Yace "To shine dai har yanzu ba mu gama tattaunawa da Hajiya ba." Hawayen da nake ta riƙewa ya kwaranyo min kafin in goge har ya gansu, ya tashi ya je ya kulle ƙofar ɗakin shi ya zare makulin ya saka a aljihu. Ya zo ya zauna kusa da ni ya saka hannu ya ɗago fuskata ya saka yatsa yana share min hawayen yace "Nasan zaki fice ki tafi dakin ki ne kije kiyi ta kuka, bayan kin yi min alƙawarin baza ki ɗaga hankali ba." Na kirƙiri murmushin yaƙe, hawayen suna sake kwaranya,nace kayi hakuri ina ta ƙoƙarin inga cewa na tsaida hawayena amma na kasa. Yace, "Karki damu fa, ko mata nawa zan kawo Baby kinsha gaban kowace a zuciyata, kuma Baby ke ce mace ta farko da nake shakkar in ganta a damuwa bayan Hajiya. Ki tattala hakan Baby ina da tabbacin za muyi rayuwa mai tsawo da tsawon rai." Ya ɗago fuska ta muka haɗa ido "Kinsan me yafi damuna?" Na girgiza kai, ya kai hannu ya ja doguwar rigata ya zura hannu ya shinfiɗa shi a tafin cikina, na ƙosa inga kin samu ciki,na fara tsoron ko akwai wata matsala." Nace duka wata uku da kwanaki ai ba 'a jima ba." Yace "An jima mana, mace bata wata a gidan nan sai ta ɗauki ciki fa." Nace to muyi addu'a jinkirin ya zama alkhairi kuma duk ga yara a gidan. Yace "Wallahi ban taɓa samun kai na da son ganin mace da ciki kamar ke ba." Nace Allah ya bamu masu albarka. Koda ya ci gaba da sarrafa ni domin biyan buƙatar sa yanayin kishi bai barni na taimaka masa ba kamar yadda muka saba, hasali ma hawaye na na ci gaba da zubdawa har ya samu kansa. Ya dube ni yace "Yau dai ni nayi kiɗa na da rawata ko Baby?" Nace kamin afwa da uzri. Yace shike nan muje muyi wanka. Gaskiya ina da kishi mai yawa ƙiriƙiri na kasa bacci kuma duk da na tashi na yi sallar dare na faɗawa Allah damuwa ta hakan bai hana zuciyata saƙamin cewa in nemi saki daga gare shi ba. To amma ya zanyi da wutar sonshi da ke ruruwa a zuciyata. Ranar Lahadi tamkar ranar salla ce a gurina tun safe kowa na gidan ya fahimci hakan Shamaki ya ce to in har Umma zata zo da wuri zata iya samu na, nace bari in kira inji. Jamila na kira na tambaya ta ko da wuri Umma zata zo, sai tace sha biyu zata zo ta dawo ƙarfe biyu. Ɗaya saura wayar ɗakina ta yi ƙara,na ɗaga Hajiya tace "Ki zo ga Ummanki da murna nace To. Na fito da sauri ina shiga sam na manta da kowa ita kawai idanun na ke gani a falon naje na rungume ta ina faɗin Oyoyo Umma. Tace "Kai jama'a to ɗagani mana. Na tashi na zauna muka gaisa, na kalli Hajiya wadda ta zuba mana ido tana murmushi. Tace "To kije ki ce Juma ta kawo mata abin sha da abinci." Nace Umma ina su Jafar ke kaɗanki wai ki ka zo? Tace "Abbanku ya hana." Nace Allah sarki ina son in gansu. Na tafi gurin Juma nace a kawo wa Ummanmu abinci. Tace "Au dama Ummanki ce baƙuwar da Hajiya ta sa ayi wa girki na musamman? Lallai ke da alamu kina samun shiga a gurin Hajiya,ko kuma ku ƙarawa malamin ku sadaka domin ina ganin canje canje a gurin Hajiya." Nace ki kawo mata abincin yanzu. Tace "To za 'a kawo yanzu, ɗakin ki za"a kai ko kuwa gurin Hajiya? Ina ki ke ganin zai fi dacewa? Na tambaye ta. Tace "Tunda ki nemi shawara za a baki tsaya kinibibin cewa a kawo musu ɗakin ki ba, a kai mata gurin Hajiya su yi hirar su ta manya. Sannan kar ki tsoma musu baki wai domin kinga Ummanki, abu na gaba ki jira har sai Hajiya da kanta tace Ummanki taje ta ga ɗakinki. Nace Na gode Baba Juma. Na dawo na zauna a gefe shi Shamaki ma ya shiga ciki. Nace Hajiya suna shiryo abincin. Hajiya ta zura min ido tana tambaya ta. Ɗakin ki za'a kai mata ne?" Nace A"a nan dai gurin ku ko Hajiya..Juma ta zo tana jerewa. Umma tace kayya sai da na gama abinci na taho a ƙoshe nake. Nace haba Umma ai dai ko yaya kyaci abincin gidanmu. Hajiya tace "Ai wajibi ne ma ki ɗauki plate ki zuba mata, sai kije mijinki ya shiga ciki zai shirya ya tafi kasuwa." Umma ta yi karaf ta ce kije ki sallame shi zanci kafin in tafi yanzu dai bana jin yunwa. Nace to. Na tafi da sauri, na same shi yana waya da wasu kwastomomin shi ya ce zai fito nan da awa ɗaya. Na buɗe durowa na fara zaɓo mishi kaya, ya kamo ni "Zo nan mana kinsan yadda ki ka fito da murna da tsalle ki ka faɗa jikin Umma ina kallon ki sai naji kawai ina bukatar ki, dama yanzu zanje in kira ki. " Cikin mamaki nace haba dai aiko ka ɗaga min ƙafa yau ɗaya Ummana ta zo tana gidan fa kuma ba jimawa zata yi ba, yace ai nima ba jimawa zamu yi ba... KARSHEN LITTAFI NA BIYU Mu hadu a littafi na uku Taku Halima Abdullahi K/Mashi.