HAIHUWA DA HANJI (A True life story) FATIMA MUHAMMAD GURIN *GUREENJOH* *FREE BOOK* *TSOKACI* Wannan littafi nawa mai suna HAIHUWA DA HANJI ban san ta ya zan fasalta muku ba amma tabbas yayi matuƙar shan bambam da sauran littatafai na don labari ne na wata baiwar Allah da ya faru a gaske, kashi saba'in cikin ɗari duk ya faru sai kaɗan da za mu ƙara ta yadda zai ƙayatar ya kuma isar da saƙon da muke buƙata ba tare da tangarɗa ba. I promise it's going to be a hit kar ku ga don free ne yana daga cikin labaran da na jima ban rubuta irin shi ba don haka ku shirya shan karatu domin duk wacce bata karanta ba an barta a baya. *GARGAƊI* haƙƙin mallakar HAIHUWA DA HANJI na Fatima Muhammad Gurin ne ban amince ba ban lamunci a sauya min labari ko ta wani ɓangare ba ko a yi amfani da shi ba tare da sani na ba. *SADAUKARWA* Na sadaukar da littafin HAIHUWA DA HANJI ga ɗaukacin makaranta littatafai na. *001* Wani irin ruwa ake tsulawa kaman da bakin ƙwarya, kusan duka bil'adama suna kwance lub cikin tattausan katifa lulluɓe da bargo suna bacci kaman yadda dare ya zama mahutar bawa amma ita tana duƙe a kitchen ɗin dake tsiyaya saboda rashin kyaun kwanon da aka lulluɓe kai da shi. Wuta ne take hurawa Dukda bayanta dake ta jiƙewa har hakwaranta suna haɗe wa saboda sanyin dake shigarta hakan bai sa ta damu ba sai ma ƙara mayar da hankali da ta yi ga haurawar da bata sarara ba sai da ta ga wutar ta kama yadda ya kamata, babbar tukunya ce da za'a iya naɗe ta a sanyata ciki kuma tsaf ya ɗauketa saboda rashin ƙiba da kumarinta ta shiga kokawar janyowa da ƙyar ta ɗora bisa murhun kan ta nufi wani bokiti ta fara aikin ɗibo ruwa a kimtace tana zubawa sai da ta tabbatar yayi yadda ta saba kan ta rufe ta fito, kifi ɗanye da suke sanyawa cikin ƙanƙara a wani babbar kula ta juye ta shiga wankewa don an riga an yi mata yanka tun jiya da Magrib a bakin kasuwan, sai da ta wanke tsaf ta ɗauko wani tukunyar ta zuba su sai a lokacin aka soma kiraye-kirayen sallah daga chan nesa. Na yi mamakin yadda ko tsoro babu a fuskarta haka take ayyukan nan cikin ruwa a take ta sake haɗa wani murhun ta ɗora dahuwar miyan kifin nan, sai da ta tabbatar komai ya mata yadda take so kan ta shiga tattaro kwanukan gidan don ta san in ta bari ma gari ya yi haske ta shiga uku, wanke wanke take sauri-sauri yayinda ruwan da ya koma zuba chab chab ya cigaba da jiƙata, har ta gama jikinta babu inda ba ya kakkarwa sauri sauri ta wanke shinkafa ta zuba cikin tukunyar farko kan ta yi alwala har kuma lokacin babu mahaluƙin da ya leƙo a gidan Dukda kuwa wasu masallatan ma har sun idar da sallah. Akurkin ɗakin da shi ne nata a gidan ta duƙa ta shige ta cire kayan jikinta bakkon kayanta ta janyo da kyar ta zaƙulo wata kodaddiyar doguwar riga ta saka ta janyo hijabinta ta ɗora tare da tada sallah, ga mamakina tsaf ta gabatar da Sallar ta yadda addini ya tanadar, bata jima tana azkar ba ta fito don gudun magana amma bata tsira ba domin a kitchen ɗin ta tarar da Inna larai da sauri ta duƙa ƙasa "Ina kwana inna?" Kallonta tayi ta taɓe baki ta buɗe tukwanen ganin miyan ya yi ta juyo gareta "Uban me kika shiga ɗaki kike yi har miyan nan ya nuna saura ƙonewa baki shirya kwashewa ba? Asara kike son ja min ko?" "A'a inna sallah ne na je na yi" Tsaki ta ja tare da nuna mata kular da suke kwashe miyan tallar, ta je da sauri ta ɗauko inna larai ta kwashe tsaf kan ta ɗaura dumamen gidan a murhun, ita kuma ta wuce ta ɗauko kular kwashe shinkafa ta taho ta janyo ledar sugar ta buɗe a cikin kular kan ta shiga kwashewa turirin na Dakar ta yana ƙonata yadda ta saba har ta gama duk sanyin da ake ta jiƙe jagwaf da gumi, kwanukan tallarta ta cigaba da haɗawa a wani bokitin fenti har ta gama filate na roba da ruwa da gutsuren dollof da take wanke plates idan ta sayar aka ci aka dawo mata dashi. "Je ki bugawa su Iro su zo su ɗaura miki a baro su kai miki yanzun nan" Da to ta amsa cikin sanyinta ta nufi ɗakin na yaran mazan ta shiga bugawa, sai da ta kwashe sama da mintuna ashirin tana bugu da ƙiran suna kan wasu matsakaitan samari biyu suka fito ɗayan ya sa hannu ya hankaɗeta sai da ta faɗi ƙasa. "Don uban ki bamu hana ki wannan bugun bala'in ba? Shegiya kullum ba ki da aiki sai na uzzurawa mutane ko wani farar safiya..." "Ɗahiru ƙaniyar ka...! Kun wuce kun zo kun fitar min da abinci ko sai kun janyo min asara?" Babu ruwanta da sun yi sallah ko ba su yi ba damuwarta kawai su kai mata kayan sana'ar ta. A hankali ta miƙe tsaye tana kaɓe jikinta dama ta sani ba dai a yi musu faɗa a kan an ci zarafinta ko an zalunce ta ba, kowa a gidan na ganinta tamkar juji da in sun kwaso sharar su babu inda suke zubawa sai bisa kanta. Sumsum haka ta taho suka kama suka ɗora suna ta mitar da kullum safiya sai sun yi haka har suka fice, tana shirin fita daga gidan kenan Inna larai ta kwala ƙiran sunanta. "Afifah Ke!" Waigowa tayi da sauri kuma cikin sanyinta "Saura in ga ba daidai ba wallahi sai na lahira ya fi ki jin daaɗi kuma kika sake kika ci kai ko lasa kika yi Allah ya isa ban yafe ba ki je ki dawo ga dumamenki nan zan ajiye miki" Girgiza kai tayi fuskanta ɗauke da murmushi mai nauyi da ciwo ta amsa da "Toh" Kan ta fice daga gidan. A inda ta saba zama gefen rumfar masu tura finafinai nan ta zauna bayan sun sauƙe mata suka buɗe suka cika fillet biyu idanunta cike da hawaye tace "Iro wallahi in..." "Na uwarki ne ko na ta mu uwar? Ina ruwanki? Kuma wallahi ki sake ki faɗa mata ki ga yadda zamu yi da ke Annoba kawai" Da ƙarfi ta runtse ido sunan ba wai sabo bane a gareta sai dai a duk sadda aka ƙira ta da hakan ta kan ji zafi da ciwon fiye da ɗanɗanon maɗaci a kan harshenta. "Mai shinkafa sa min na ɗari uku..!" Haɗiye abin da ya taso mata tayi ta karɓi kudin ta saka a Jakan ƙugunta kan ta fara zuba shinkafar kaman ko yaushe fuskanta babu ɗigon fara'a ko sassauci ba kuma don komai ta ɗauki wannan mataki ba sai don kare mutuncinta. Hakan da take ya sa maza dayawa masu kawowa 'yan mata yan tallah wargi basa samun dama kowa ya santa duk tsiyarka tana da kwarjinin da in ta tsume hakan babu mai iya kawo mata wargi... Saboda tsafta da kuma natsuwarta yasa dayawa suke tururuwa wurin sayan abincinta. Ita ɗin annoba ce kaman yadda wasu ke ƙiran ta dayawa sun santa a Mayya! Dukda ita bata taɓa sanin menene maitar ba amma ta wurin kasuwanci su kan saya abin hannunta don ko babu komai akwai zaƙin hannu muddin ita tayi girki. Kan ka ce awa biyu duk ta sayar da abincin tas ta janyo baro ta ɗora kulolin a kai tana jin jiri na fusgarta saboda rabon ta da abinci tun jiya da rana gashi yanzu ana neman goma da rabi, haka ta turo wheelbarrown ta nufi gida... Razana tayi ta daka tsalle tayi baya sun saba yi mata hakan sai dai ta kasa sabo ita "Ina kudina?" Inna larai ta miƙa mata hannu a zauren wanda ko kanta bata gama sanyo wa ba, Jakan ta sunce ta miƙa mata a wurin ta zazzage ta kirga ta ga riba yadda suka saba samu ta saɓi kayanta ba sannu bare na gode tayi cikin gida abin ta, Afifah ta bita da kallo har ta ɓace kan ta turo baron zuwa cikin gida ko sauƙe kwanonin bata yi ba ta nufi bakin kitchen inda inna larai ɗin ke zaune ta duƙa "Abincina fa inna?" "Laaaa kin ga mun manta da ke wallahi ina fa ta zuci zucin ajiye miki" Runtse ido tayi da ƙarfi tana danne hawayen dake taso mata idan da sabo ya ci a ce ta saba, kusan koyaushe za su yi rabon abincinsu muddin bata gidan to za'a ce mata an manta da ita ne, wani lokacin ma sai an sauƙe sai a aiketa kan taje ta dawo an rabar kuma a hana ta, hanjinta har murɗewa suke saboda yunwa amma ya zata yi? Miƙewa tayi ta nufi hanyar akurkinta inna Asabe ta kwala mata ƙira daga cikin ɗakin ta "Ina za ki da baki karɓi kuɗin nawa aikar ba?" Bata ce komai ba ta tsaya daga kanta leda da ke kunshe da kuɗi ta jefa mata a fuska "rashin kunya za ki min ki tsaya min kerere bisa kai? Kin ɗauka kin wuce ko sai na tsinka miki mari?" Duƙawa tayi ta ɗauka ta fice daga gidan ko ɗakin bata shiga ba ta riga ta san me zata sayo, ko kan ta dawo har inna Asabe ta gama tuka tuwon tallar tata na dare, ita ta zauna ta malmala tana jin kanta na sarawa ayyukan sun fi karfin shekarunta amma ya zata yi? Mutum ɗaya take da shi a duniya Aunty zee ita ma kauyen gaba da su take kuma ta kan kwana biyu bata leƙo mata ba bare ma hakkin riƙe ta na ga dangin mahaifinta ne ita kuma ga abinda Allah ya bata, sai dai ta tashi tayi sallah har ta gama malmalar tuwon na dubu goma sha biyu kaman yadda suka saba ta ɗora miyan ta kala biyu da Alaiyahu da kubewa, bayan ta gama ne inna Asabe ta tarfa mata sauran ƙasan tukunyar tukun a cikin tukunyar miyan Alaiyahun da ta gama kwashewa ganin sai kashe jiki take saboda yunwa bata son abinda ya samu kayan tallatarta sam. Sai da tayi wanke wanke tas har da kwanukan safe na tallar inna Larai kan ta shirya ana kiran Magrib tayi sallah ta fice bakin kasuwa, yanzu ma bata kula kowa abincin kawai take sayarwa har wuraren takwas ya ƙare ta tattaro ta dawo gida dama tun shidda ta sayi kifin miyan safe ta ba almajiri ya kaiwa inna Larai za ta saka cikin ƙanƙara ji take kasusuwanta kaman ana sarawa, kuɗin kawai ta ba inna Asabe ta wuce ɗaki ta kwanta idanunta na kallon sama, shikenan ita kuma a haka rayuwarta zai cigaba da tafiya? Shikenan ita kuma haka za ta ƙare? Don dai ta san kap kauyen dutsen-wai babu namijin da zai tare ta da sunan soyayya babu kuma gidan da za su amshe ta yadda ake ganinta annoba kuma duk gidan da ta shiga sai ta wargaza kuma sai an yi mutuwa kan ta fita tayi zurfi cikin tunanin ta kawai taji ana dukan kyauren palangen dake kare kofar akurkin da ɗan banzan ƙarfi sai da ta razana ta miƙe tsaye ba tare da ta sani ba. 🖤Gureenjoh🖤 HAIHUWA DA HANJI (A True life story) Fatima Muhammad Gurin (Gureenjoh) Wattpad-Gureenjo6763 Arewabooks-Gureenjoh *FREE BOOK* *002* Nannauyar numfashi ta sauƙe sai kuma ta fita daga tsoro ta shiga fargaba, kawu ne! Me ta yi? Jikinta a sanyaye ta miƙe tsaye ta turo kofan ta fito. "Iskancin naki ya kai ina ƙiranki kina ji na ki yi min banza ko? Ko har kin tafi meeting naku na cin ɗanyen naman mutane ne?" Girgiza kai ta yi tana wasa da yatsun ta murya na ɗan rawa ta furta "Ka yi haƙuri kawu bacci na fara ne" Tsaki ya ja yana jefanta da mugun kallo, babu yadda ya iya ne kawai yarinyar ke zaune gidan shi in ba haka ba babu abinda zai sa ya ajiye makashiyar mamarshi da 'yan uwanshi har ya ke bata abinci tabbas da ana kashe mutum a sha a banza da tuni ya yanke wuyanta ya jefar da gawar daji tsuntsaye sun cinye, duniya in akwai wacce ya tsani ko inuwarta ya gani ya biyo bayanta. "Ba dai a mawankin chan za ki bar mana kwanuka su kwana ba kan safe duk shedan ya bi ya fitsare mana kwanuka? Oh ko so kike duk ki kashe mu ne ki huta?" Lip ɗinta na ƙasa ta ɗan datse a hankali kan ta saki ta furta "Kayi hakuri zan yi" Ya ja tsaki kan ya juya ya wuce ɗakin inna Asabe. Mawankin dai ta wuce akwai ɗan guntun omo haka ta fara wanke wanken idanunta kaman za su cire saboda raɗaɗin bacci har kifewa take yi bisa kwanukan tana tashi sai da kusan duk kowa yayi bacci a gidan kan ta gama kifewa ta wuce nata akurkin sanyi kaman zai kasheta ta shige cikin zaninta bayan ta sauya hijabi zuwa busasshe dukunkune haka tayi baccin. Kaman jiya yau ma dai kowani ɗan adam na kwance yana bacci haka ta fita tsakar gidan ta shiga aikin abincin tallar inna larai. Ba don ba'a sabo da wuya ba zata iya cewa wahala ya riga ya zama jininta, bata san yadda zata fassara rayuwa ba sai dai ta san ƙaddararta mai matuƙar zafi ne da ta kan rasa sanyi ko sama ko ƙasa a duk sadda ta rura wutar ta. Bata da farin ciki ko ɗaya bata da mai tambayar damuwarta ko ciwonta har ma da bukatuwarta waenda suke tare da ita amfana da ita kaɗai suka iya amma ita bayan mafaka da kwanon abinci sau ɗaya a wulakance bata anfanuwa da su ko ta wani ɓangare, manyan su zaga, matasan su daka su kuma hantara yaran su wulakantata bata da bakin magana saboda ita ɗin ta riga ta zama annoba... Eh annoba zata ƙira kanta kaman yadda kowa ke kiranta an haife ta da rashin sa'a tunda tana ciki watanninta basu wuci biyar ba Allah ya karɓi mahaifinta, a wurin haihuwar ta Allah ya karɓi mahaifiyarta ta zama cikakkiyar marainiya daga ranar da ta faɗo duniya, kakarta ta wurin uba ita ce ta raine ta kan madara ta bata tarbiya ilimin addini da boko har ta shekara takwas ita ta sani a matsayin uwa kuma uba, ta samu gata na iya tsawon lokacin da tayi da kakarta har makarantar gomnati na boko ta sanya ta kan kwatsam mutuwa ta yanke wannan ƙauna tun daga sannan aka fara jita-jitar ita ɗin Mayya ce! Kuma duk wanda ta raɓa zai mutu. Tsangwama ya fara yi mata yawa a hannun ƙanwar babanta da ta koma Inna Amina ta sha baƙar wahala kasancewar inna Aminar ma cikin gidan yawa take, mijinta kuma ba wai ya karɓe ta bane zaman dole take mishi a gida hatta abincin gidan bai amince a saka mata ba duk abinda aka sanyawa inna Aminar suke taɓawa a tare, ta samu innar tata da ciki a lokacin kawunta ya ƙi yarda ya ƙarbe ta tunda su uku kawai kakarta ta haifa. Kawu ne babba sai babanta tukuna innar dole dai wurinta take lallaɓa wa rayuwarta. Wata rana inna Amina ta tashi da nakuda babu wani cima mai kyau, babu cikakken kulawa da ya kamata mace mai ciki ta samu, bata taɓa zuwa awo ba ana rayuwa ne cikin wahala haka ta tashi nakudar a gida aka kira unguwarzoma ta ci azaba ko da ta haihu babu rai ita ma bata jima ba jini ya balle mata ko kan a ce an yi wani yunkurin Allah ya karɓi abin shi, ko gawar inna da jaririyarta ba'a binne ba aka sanya Afeefah gaba da zagi, cin mutunci, baƙaƙen maganganu babu irin wanda ba'a jefeta ba a lokacin da take jin tashin hankali da damuwar rashin innarta Aminan. Ta ga mutuwar kaka amma bai kaɗata kamar na inna Amina ba saboda yadda ta mutun a wulakance cikin sakacin miji da kishiyoyi ta yi kuka kaman babu gobe, har jifan ta da dutse ake yi in ta fita a haka kawu ya dawo da ita gidan shi tana da shekaru 10. Matanshi basu karɓeta ba, babu wacce take yarda har yanzu ta shigar mata ɗaki ko na yaransu dole aka buga mata keji don ba shi da maraba da keji aka sanya buhu aka bata taburma saboda kar ta kashe musu 'ya'ya, bata sani ba ko tabbatar ta mayyar ce ta sa yanzu shekara shidda kenan da dawowarta gidan kawu bayan ɓari da matan suke yi babu wacce ta sake haihuwa, sun yi duka sun yi zagin duk a banza wai an tsikari kakkaura ita bata ma san ta yadda ake yin maitar ba, wani lokaci har ta kan yi adu'ar ya tabbata ita ɗin Mayya ce don tana so ta ba su kyautar kanta duniyar bata da anfani a gareta. bata ƙara zuwa makaranta ba ko na boko ko arabi tun bayan mutuwar kakar ta sai dai ta ga wasu da kayan makaranta, ta zama boyi boyi abin wulakantarwa, abinci wannan da kyar ake bata a gidan kan suka fara ɗora mata tallah ganin tana da wannan farin jinin ya sa suka dage kuma ake kishi a kanta don kaman yadda suke raba kwanan mijinsu haka suke raba ta. Dole kuma a rana idan ta yiwa wannan sai ta yi wa ɗayar idan ta sayarwa wannan ko kwana zata yi waje sai ta sayarwa ɗayar kan ta dawo gidan in ba haka ba ta shiga uku, bata sani ba zata tabbata a haka Ko wani sauyi zai iya shigowa rayuwarta? Ita ɗin Mayya ce da gaske? Har yanzu tambayar da ita karan kanta bata iya amsawa kanta ba kenan bare ta amsawa azzaluman mutanen da suke zagaye da ita. "Ke!!!" A ɗan firgice ta ɗaga kai sai ta ga wani matashi na miƙa mata kudi "tun ɗazu ina ta magana kin yi shiru kaman bakya duniyar? Saka min na ɗari biyar" Abincin ta shiga sakawa shi ne ma na karshe don wuraren sha ɗaya na safe ne, bayan ta saka mishi ya koma cikin matasan da suke tare ya shiga ci ita kuma ta fara tattare wurin cikin natsuwa da sanyinta sai da ta gama zuba komai cikin wheelbarrown tana jiran matashin ya gama ya bata plate sai kawai ta fara jin hayaniya na tashi, ɗago kan da zata yi sai ta ga wannan saurayi ne dafe da ƙirji yana tari sossai da sossai har filate ɗin ya faɗi ƙasa abincin ya tarwatse ya bi abincin yana tumurmusa a ƙasa, kan kace kobo wurin ya cike da mutane wasu na cewa ya mutu wasu na cewa da sauran ranshi. "Me ya ci ne? Me ya same shi?" Abin da mutane dayawa ke tambaya kenan, ita dai Afeefah na kafe a wurin ko motsi ta kasa sai gangar jikin da mutane suka yi wa zobe kwance ta zubawa idanu kaman daga sama ta ji Muryar wani na cewa "Daga fa sayan abincin yarinyar chan kun ga bai ma gama ci ba...! Ku taimaka mu kaishi asibiti kar ya rasa rayuwarsa kumfa ne a bakin sa" Cikin jimami ya ƙarasa Wata murya taji tana cewa "hohoho asshaa dama na san aje aje sai ta fara yiwa mutane dauki ɗaiɗai shiyasa ban taɓa sayan abincinta ba, yarinyar da riƙaƙƙiyar Mayya ce an ce ma ita ce mataimakiyar shugaban Mayu yanzu?" Ko motsi bata iya ta yi ba taji an damketa zuciyarta kaman zai fito waje ba na tsoron abin da mutane zasu iya yi mata ba sai na tsananin tsoron mutuwa, mutuwa na daga cikin abinda a yanzu yake gigitata dole duk mai imani ya tsorace mutuwa a yanzu yaron nan ke mata magana a yanzu ana cewa ya mutu? Ta yaya? Meyasa sai da ya sayi abinci a hannunta? Wani mai ƙirar ƙarfi ya hankaɗata tsakiyar mutanen "Ke tsallakeshi sau uku ki sakar masa kurwa yanzu wallahi ko mu sheƙa ki barzahu.." Yayi maganan da karaji yana zaro wuƙa mutane suka fara kananun maganganu masu zaginta na yi, wasu har labari suke bayarwa na ta kashe iyayenta ai maitar gado ne tun a ciki ta fara kisa, hawaye masu zafi ne suka shiga gangaro mata a sadda take tsallakeshi a dole, kalaman da suke shiga kunnuwanta sun yi mata girman da ba zata iya ɗauka ba, abin tashin hankalin ma shine yaron bai tashi ba, ya tabbata ya riga ya rasa ransa ko kan ta gama fahimtar kanta har tayi wani yunƙuri an rufe ta da duka, ko yunkurin kare kanta bata yi ba don a yanzu ita ma ta fi ƙaunar mutuwar da rayuwa, da kyar wasu dattijai suka kwace ta fuskanta har ya fara sauya kamanni wasu sassa na jikinta na zubar da jini, kwanukan inna larai da kulolinta an yi daga daga da su, ko kasheni ka ɗaukanta (lalitar kuɗi) bata gani a jikinta ba. Wani irin deep kuka take yi mai taɓa rai, dattijon ta kalla "Don Allah baba ka bar su su kasheni kawai nima ina so in huta, don Allah ku bar ni su kasheni" Abin da take ta maimaitawa kenan tana gunjin kuka ya riƙo hannunta "Ki natsu yarinya babu mai kashe ki, shima kwananshi ne ya ƙare ya mutu kiyi hakuri ki tashi mu raka ki gidan ku" Cikin in-inaa take cewa "in naje gi..gidan ma ba..ba tsira z..Zan yi ba kuɗin inna larai da kwanukan ta duk babu" Ta sake rushewa da kuka, tausayinta ne ya kama su suka haɗu suka tasa ta gaba har gidan, kawu suka fara nema ko da ya fito da kallon tsana ya shiga bin ta. "Yau kuma magana kika janyo min ko? Kayan uban wa kika sata ko uban wa kika kashe??" Dattijo ɗaya daga ciki yace "A'a malam labaran ya kamata ka fara tambayar raunin jikinta ne amma damuwarka wani abu daban? Ka san yaran zamani da kansu a koyaushe baya gayamusu daidai akwai wani yaro da ya sayi abincin 'yar wajenka yana cikin ci sai Allah ya turo da ajalinshi a take ya tafi shine suka yi yunkurin kasheta a cewar su ita ce ta cinye kur..." Tuni ya katse su "Ai da kun barsu don ni baku burge ni ba sam, da kun barsu don ko rantsuwa nayi ba zan yi kaffara ba ita ce nan ta kashe shi, sai ki shiga ai ki jira zuwan iyayenshi tunda ba kowani mahaukaci bane zaki mishi asarar rai ya barki ki sha ba" "Ashshaa amma...." "Babu ruwanku! Tunda kun kawo ta zaku iya tafiya" ya cigaba da mita kaman zai ari baki yarinya ba jari zata kawo mishi ba, ba auruwa za tayi ba babu wani amfanin da take mishi sai cin abincinshi amma kullum bacin ranta ya fi na kowa a ranshi. Dattijan suka juya suka tafi ita kam kanta ƙasa zuciyarta na wani irin karta, hawaye kuwa sun ki kafewa a idanunta kafafunta da suka matuƙar yi mata nauyi take kokarin ɗaga wa ta shiga cikin gidan taji an fusgo ta har tana taga taga zata faɗi wuyan hijabin jikinta aka shaƙo "Ina kudina da kayana?" Kakari take don ko numfashi ta kasa shaƙa, idanunta da suke manya suka sake fitowa ainun sun rine sun chanza gabaɗaya. Inna larai ganin zata yi kisa ya sa ta Hankaɗata bata damu da kokawar saisaita numfashin da take tayi ba ta daka mata tsawa "nace ina kuɗina?" "In...nn..a B..ban san ya ak...a yi ya fice daga ji..jikina B.." Hayewa ruwan cikinta tayi ta shiga ɗirkarta kaman an aiko mata ita "kaman kuwa yadda ya fice baki sani ba haka sai na rabaki da numfashinki baki farga ba, wlh dukan kuɗina yau sai na yi miki shi" Ko karfin kare kanta bata dashi sai da dukan yayi yawa ne kawu Labaran da ke kishingiɗe yana sakace haƙorinshi ya fito ya ɗaga inna larai "ke kar ki yi min kisa a gida" Yana kai nan ya juya ya bar wurin ta cigaba da sababi da zage zage karshe ta tafi ta barta nan yashe. Yaran gidan bayan sun gama kwasar dariya kowa ya kama gabansa Inna Asabe ma na girki tana zaginta da tsine mata don yau ta yi mata asarar tallar yamma tunda yanzu ko ta fita ba su da tabbacin akwai mai sayan abin hannunta irin wannan suncewar zani a kasuwa da tayi musu, ta fi mintuna goma a kwance a wurin kan da rarrafe ta shiga akurkinta ta faɗi bisa taburma tana kuka kaman ranta zai fita. Ko mintuna biyu bata yi da shiga ɗakin ba tana yashe a inda take ta soma jin hayaniya tamkar ana yaƙi, idanunta sun kumbure ko iya buɗewa da kyau bata yi, bata san ya aka yi ba sai ji tayi an janyota tamkar tsumma an fitar da ita, sama sama take jin mutane na ta hayaniya tana hangar sanduna da makamai na tashi sama ana ikirarin kasheta kaman yadda ta kashe musu ɗa matashi, bata san ashe rigimar har su kawu ya shafa ba don sun rantse in ba'a fita da ita ba gidan gabaɗaya za su ƙona, tashin hankalin da bata taɓa shiga ba ta shiga a ranar, bata san ya aka yi 'yan sanda suka iso wurin ba don ana ta janta tamkar kaya ko takarda Muryar kawu na ihun kar su ƙona masa dukiya ita suke so don haka ga ta nan su kashe ta. Fusgar ta aka yi aka wulla ta motar 'yan sanda suka ja suka yi ofishin su da ita... 🖤Gureenjoh🖤 HAIHUWA DA HANJI (A True life story) Fatima Muhammad Gurin (Gureenjoh) Wattpad-Gureenjo6763 Arewabooks-Gureenjoh *FREE BOOK* *003* Bayan tsawon lokacin da ba za ta iya cewa gashi ba ta ji sauƙar ruwan sanyi a kanta duk da ta farka sai dai bata da kuzarin ɗaga ko da yatsar hannunta ne. " In ba kema da ja wa kai ba ina ke ina cin maita don janyowa mutane bala'i ki mutu a ce ai ba ma aikinmu ne yadda ya kamata. tashi my friend" Ya ƙarasa yana kai mata kafa. Laluɓe take har ta samu ta miƙe zaune gajimare ya rufe mata ido bata iya ganin komai. Maƙogoronta da ke bushe ko miyau ba ta iya haɗiyewa sai kartar ta yake da kyar ta buɗe baki ta ce "R..ruwa..a don Allah" Ruwan ya tura mata ta ɗauka ta afa a baki har kwarewa take sai da ta sha sossai cikinta ya murɗa don dama babu komai ciki ai sai amai tana jin ɗan sandan na zaginta amma ba za ta iya tsayarwa ba ya riga da ya zo, a lokacin idanunta sun washe tana gamawa ya tasa keyarta ta kwashe ta share wurin cikin layi. A lungun cell ɗin ta raɓe tana ta aikin riƙe ciki saboda yunwa, ɗaya dan sandar ya taso yana ƙare mata kallo "Ya dai?" "Yunwa nake ji" Murmushi yayi yana gyaɗa kai yana sake ƙarewa halittarta kallo Dukda rama ya yi mata yawa ainun albarkatun jikinta na daidai shekarunta ba su ɓuya ba sam. "Zan sayo miki abinci amma kin san gomnati ta hana aikin banza ko? Nima za ki rama min" Sam bata wani fahimta don yunwa ba ta da hankali samm kai kawai ta gyaɗa ya fice chan sai gashi da filate ya miƙa mata ta fusga ta shiga ci hannu baka hannu ƙwarya sai da ta fara koshi tukuna ma ta fahimci ashe gari ya waye kenan a cell ta kwana gashi har ana batun ƙiran sallar azahar tsabar rashin gata babu wanda ya neme ta, ta tabbatar ko shekara zata yi nan kawu ba zuwa zai yi ba bare ya cire kuɗin shi yayi belinta don sun ce sai an ba su kuɗin mai za su sake ta... Bayan ta gama ta roƙi za tayi sallah basu hanata ba ta rama duk waenda aka bi ta. A nan ta cigaba da zama ita daya har dab Magrib wani matashin ɗan sanda ne ya shigo yana dubanta "Ya Sunanki?" "Afeefah" "ba ki da kowa ne da zai zo yayi belinki?" Ta girgiza kai "Ni marainiya ce kawu na kuma na san ba zai taɓa zuwa ba ko shekara zan yi" 'dan shiru yayi "Afeefah za ki iya komawa gida da kan ki?" Ta gyaɗa kai "tashi ki tafi to zan biya kuɗin belin naki, bana so dare ya sake samunki a nan muna da gurɓatattun 'yan sanda bare har kin bari kin ci abin hannun kopur DanJuma sai ya dawo, kuma ba ni da ƙarfi ko ikon kare ki" Hawaye ne suka cika kumburarrun idanunta ashe akwai masu zuciyar imani da tausayi a cikin 'yan sanda? Godiya tayi ta mishi har da kuka a lokacin da zata fita ta ce "Menene sunanka?" "Sa'adu. Sa'adu Rabi'u" "Allah ya dube ka ya shiga cikin lamuranka ya dafa maka" Amsawa yayi ta fice da sauri lunguna tayi ta bi a tsorace kar ma ta haɗu da kopur Danjuma har ta isa gida. "Uban wa yayi belinki?" Kawu dake kofar gida ya daka mata tsawa "Su...su suka sake ni" Takalman shi ya wuwuro ya jefa mata "shegiya natacciya dama shiyasa ake cewa mutum maye mana in ya cika naci, kin rantse sai kin kasheni ko? To kafin nan sai na yi ajalinki marar anfani kawai" Da gudu ta shiga gidan don ya miƙe ya biyo bayanta kaman zai faɗi. Ɗakinshi ya shiga ya haɗo tarkacen da ya karɓo na kare kai daga sharrin Mayu yayi ɗakinta dorinarshi ya samu ya rufeta da duka wai na hawan jinin da ta saka mishi jiya ta kusa ja mishi asarar rai da dukiya babu wanda ya kula su duk ihu da neman agajinta sai da ya gaji ya kyaleta. Ya sa aka kawo mishi garwashi ya turbune su da uban hayaƙi mai bala'in ƙauri bayan ya gama ya tafi ya barta nan yana cigaba da sababi. Bata san iya adadin lokutan da ta ɗauka a kwance cikin yanayin ba, tun tana kuka da hawaye har suka ƙafe sai dai zuci na cigaba da zubar da kwalla cikin ƙunci da raɗaɗin da bata san ranar tsayuwarshi ba, yunwa ne kaman zai yi ajalinta hakan ya sa ta dole ta lallaɓa ta fito, yadda garin yayi shiru sossai za ka san cewa dare ya riga da ya tsala murhu ta isa akwai sauran gawayi ta dibo ruwa tana layi ta ɗora, a wurin ta zube tana kallon kicin ɗin babu alamar an ajiye mata wani abu da zata iya ci, busashen miyau da ya ƙafe a Bakinta ta lalaɓo da kyar ta Haɗiye. Sai da ruwan ya tafasa ta juye hadari ne sossai a garin don har an fara iska da walkiya sai dai dayake zuciyarta a kafe yake yasa babu tsoron komai cikin ranta ta shiga ta gasa jikinta sossai ta fito, kicin ɗin ta koma da kyar ta samu wani kanzo ta ɗan bubbuga ta zuba ruwa yayi laushi ta ɗauka ta nufi akurkinta tana da ɗan maggi da yaji da mai kaɗan ta saka a ciki ta ci bata ma gama ci ba taji sauƙar ruwa kaman da bakin ƙwarya, ko da ta kwanta baccin sai ya ƙi zuwar mata sai tunanin rasuwar yaron jiya take ko wani hali iyayenshi ke ciki? Tana kuma tambayar kanta da gaske ita ɗin Mayya ce? Da ƙyar bacci da ya fi kowa iya sata ya lallaɓo ya sace ta... Rayuwa ya ɗauki yi mata zafi a gidan fiye da baya saboda a yanzu tallar bata yi inna larai ta yi mugun tsanarta don ta karya mata kasuwa hakan yasa ko abin da zata ci a girkin inna larai gagararta yake, ba'a isa a aike ta ba haka zata dawo da hawaye saboda maganganun mutane da ma yunkurin illata ta da wasu kan yi, bautar gidan duk ya dawo kanta yanzu har girki ita ke yi musu su zo suyi rabo kuma a hanata don daga an sauƙe za'a aike ta kan ta dawo an raba in ta tambaya su ce sun manta da ita, ita dai gata nan amma rayuwar baya yi mata daaɗi ko ta wani ɓangare. ''Ina ma mutum na da zaɓi kan rayuwarsa! Ina ma a ce bawa ke da ikon rubuta ƙaddararsa! Da ban zaɓi maraici ba. Duk bala'i na san ko da kowa zai guje ni su ɗin ba zasu taɓa guduna ba" a hankali take furta hakan wani irin kewa da maraici na taso mata, har ƙasan ranta bata son yadda ta zama tamkar mujiya a cikin tsuntsaye, bata son wannan suna na Annoba da yanzu kowa ke ƙiran ta dashi... Kanta a duƙe ƙasa ruwan hawayen da bata rabo da su na sulmiyowa cikin ruwan kunfar wanke-wanken da take yi wani irin zafin da zuciyarta ke yi kaman zata fito daga madaukarta "Wai zama kika yi kina maitar da kika saba na shanye kurwuwowin mutane ba za ki yi ki kawo mini kwanuka in raba abinci ba?" Inna larai ta watso mata kalaman cikin hantara. sharɓe hawayenta ta yi, cikin mintunan da ba su wuce biyar ba ta kammala. Tattara kwanukan ta yi ta kai gaban murhu ta ja jikinta gefe ta tsaya tamkar jiƙaƙƙiyar kaza da ta rasa mafaka yayin ruwan sama. "Ungo sayo min kuka da daddawa." Kuɗin da ta wullo mata a wulaƙance ta sanya hannu ta ɗauka ta juya tana jefa singallin kafafunta masu kama da zaren lipton saboda rama tayi waje, ko da ta dawo zaune ta tadda zuri'ar gidan suna karyawa cikin natsuwa. "Ga shi inna larai" Fusga ta yi suka ci gaba da kai lomar zazzafan ɗumamen tuwon dake turiri ita da Inna Asabe "Abinci...cina fa?" Ta yi tambayar zuciyarta na rawa. Amsar da take tsoron ji ita ɗin dai ce ta ratsa kunnuwanta. "Kin ga na manta da ke a rabo, sai ki jira na rana." Wani irin raɗaɗi ne ya ziyarci idanunta tamkar wacce aka watsawa borkono. Ba ta sauya zani ba ba kuma ta tunanin za ta sauya ɗin abu ne da ta riga ta sani a kullum idan har za a raba abinci aka aike ta shi kenan rabonta ya faɗi ƙas. Ita take kallo sai dai tuni zuciyarta da ƙwaƙwalwarta suka tafi nisan kiwo, hanjin cikinta jin shi take kamar ana daddatsawa tsananin yunwar da ta kwana da ita. Ba ta da shi ba ta kuma da wanda zai ba ta babu mai ɗigon tausayinta a gidan a cewarsu mayu sun fi cinye kurwan wanda ya ji tausayinsu ko ya taimaka musu. Sauƙar ruwan zafin da ta ji a fuskarta yasa ta sakin ƙarar azaba a firgice ta miƙe daga durƙuson da ta yi a gabansu tana dirza fatar inda wani irin zafi ke ziyartar ta. A take ta ɗaile, daidai lokacin inna larain take faɗar "Wallahi kurwata kur! Maye sai dai ya ci kansa." Baya ta matsa ta sake zubewa bisa gwiwoyinta hawaye na sake tsinke mata cikin shessheƙa ta fara roƙon su taimake ta da abinci. "Inna don Allah ko da loma biyu ne ku taimake ni da ita, cikina babu komai hanjina murɗa suke, yunwa za ta kar ni." Kamar dabba haka ta sa ƙafafu ta hamɓare ta ba tare da ta ko damu da raunin ƙunar da ke jikinta ba. "Ba za ki taɓa samun nasara a kaina ba, wuce ki fara shirin ɗaura mini abincin rana." Jiki a saɓule ta miƙe ta nufi wurin murhu, a haka cikin raɗaɗin gangar jiki da zuci ta fara aikin. Bata yi nisa a aikin ba suka gama karyawa suka kai kwanukan mawanki kowa ya nufi ɗakinsa don hutawa. Ta rarrafa ta isa bigiren saboda ko ƙarfin miƙewa tsaye babu jikinta tsabar yunwar dake dawainiya da rayuwarta. Ɗan sauran wanda suka rage take kwarfewa tana afkawa a bakin salati, ta haɗe da tukunyar ta kankare ƙasan tana ci tana zub da hawayen tausayin kanta da irin rayuwar da take. Ko kula inna Larai dake mata gargaɗin kar ta yi mata lamba a tukunya bata yi ba. Ta miƙe ba don ta ƙoshi ba sai don babu wani abin da zata sake samu ta ƙarasa ta kwalfi ruwa ta afawa cikinta. A gindin randar ta raɓe cike da fatan sanyin ya taimaki zuciyarta wurin kashe wutar dake ruruwa a cikinta har take neman kai ta ga kushewarta. "Afeefah! Afeefah!!" Sam bata san bacci ya sure ta a wurin ba sai da ta ji ana jijjiga ta tare da kiran sunanta. "Lafiya kike bacci a nan?" Idanunta da ba su da maraba da na mashaya saboda gajiya da jigata ta ware tana kallon mai maganar da muryarta yayi kama da wacce ta sani da jimawa, a hankali sanyi ya shiga ratsa ta. Sanyin farincikin sanya mace guda da ta rage mai ƙaunarta kaf faɗin duniya a idanunta, tashi ta yi cikin azama da 'yar fara'a ta rungume ta. "Afeefah....!" Kiran sunanta da ta yi tare da fincikar da tayi mata daga rungumar tana ƙarewa fuskarta da ma jikinta kallo ne ta ji tamkar ta sosa mata inda ke yi mata ƙaiƙayi. Dama me neman kuka ne aka jefe shi da kashin shanu. "Wa ya yi miki wannan lahanin?" Ita dai ba baki sai kunne don haka ta ci gaba da kukanta yayin da ta shiga rarrashinta itama hawayen take zubarwa. Da ƙyar Afeefah ta yi shiru kan matar ta buɗe jakar hannunta ta fiddo biredin da ta yo mata tsaraba. Kamar mayunwaciyar zakanya haka ta afka masa da ci ba ji ba gani har tana ƙwarewa, matar ta ɗibo ruwa ta ba ta hawaye na gangaro mata, daidai lokacin da kawu ya fito shirye da alama kasuwa za shi.. "Labaran ka ji tsoron Allah, wallahi ka kwana da sanin kai ma ba ka fi ƙarfin ƙaddara ba. Rayuwa da kake yi da 'ya'yanka ƙarƙashin kulawarka ba wayonka ba ne ballantana dabararka, a yau za ka iya faɗuwa ka mutu, shin za ka so a yi wa 'ya'yanka yadda kake mata?" Kanwar mahaifiyarta ta jefa masa kalaman cikin jin haushin yanayin da ta zo ta iske Afeefar Kallon banza ya watsa mata. "Kina da gida ko Zainabu? Toh ki tarkata ta ku tafi tun kan mu yi ɓacin ɓacina kuma ki daina haɗa yarana da wannan annobar... Ni ban haifi maye ko ɗaya ba, ban kuma shirya mutuwa ba. Zaman ma da kika ga tana yi saboda ba ni da yadda zan yi ne, amma yanzu tun da ga ki Allah ya raka taki gona...!" Har ya nufi fita ya dawo ya sake kallon ta. "Af! Idan ƙarshen saduwar kenan to ubangiji ya sa can ta fi miki nan." Miƙewa tsaye ta yi a zuciye. "Zan tafi da ita Labaran, dama rashin sani ne ya sa kaza ta kwana da yunwa a saman dami, idan ka ga na mutu lokacina ne ya yi. Ke tashi mu tafi." Ta watso ma Afeefahn sauran kalaman nata tana kallonta, tun farkon rasuwar mahaifiyarta Aunty zainabu da ita kaɗai ce ƙanwar mahaifiyarta ta so karɓar ta sai dai kakarta ta ƙi har ma ya kai ga sun yi rigimar da ta sa tayi matukar fushi, sau ɗaya ta taɓa zuwa ta duba ta a gidan kakartata sai lokacin da take wurin innarta ma ta zo ta duba ta, haka ma tana gidan kawu ta zo sau biyu sai dai bata taɓa wuce awa ɗaya ba tana ganinta ta kawo mata tsaraba ta tafi don wani kauye gaba da su sossai take. Duk da chan ta san Afeefahn na cikin damuwa sai dai bata san ya kai har haka ba, ganinta a yanayin da ta sameta ya matukar ɗaga mata hankali. "Afeefah da ke nake yi!" idanunta da kaman za su faɗo ta saisaita ta miƙe da sauri ta shige akurkin ɗakin nata. Wani tunani da ya ɗarsar mata ne ya sa ta nemi gefen kayanta ta tsuguna, hawaye ne ya cika idanunta Aunty Zee ce ta shigo tana ƙarewa ɗakin kallo cike da tausayawa ta duƙa gangarta tare da dafa kafaɗarta Kaman ta karanci yanayin da take ciki da tunanin da zuciyarta ke yi. "Sau tari ƙaddarorin da ke zagaye da mu su ke taimaka mana wurin tabbatar da imaninmu ko akasin hakan, ina so ki zama tuwon hatsi mai yawan juriya, dukkan tsanani yana tare da sauƙi. Mu tafi." Taya ta tayi suka haɗa yar Ghana most go ɗinta da babu wasu kayan kirki suka fice, bata damu da ko sallaman su Baba Larai ba su ma kuma dariyar Allah ya tura ƙeya suka bi su da shi don yanzu Afeefahn bata da anfani a rayuwarsu. Tasha suka tafi suka hau mota, ita dai jikinta ya matuƙar sanyaya damuwar da ke ranta ko kusa bai ragu ba saboda tsoron kar wani abu ya sami Auntyn nata da take ji da, ya haɗu da bata taɓa shiga mota ba a rayuwarta don bata taɓa barin garin nasu ba wannan ne karo na farko, bata san akwai titi kwantacce irin hakan ba sai da suka ɗauki titin cikin garin Anchau daga kauyensu chan cikin Dutsen-wai na Kaduna state, tun tana kalle-kalle har bacci ya sure ta, sai ji tayi Aunty zainabu na tashinta tana bude ido ta ga har sun iso inda za su sauƙa ba ma su isa tasha ba don Auntyn gidan ta na daga wajen garin Anchau duk under kubau LGA of Kaduna state ne, sauƙa suka yi ta ɗauki kayanta a kai suka gangara layin har zuwa gidan, layi ne na masu matsakaitan ƙarfi da rufin asiri gidan Auntyn ba wani babba bane sai dai ciki biyu ne da parlor sai tsakar gida da take da tarin shuke-shuke. A madaidaicin parlorn ta yi mata masauki ta buɗe karamin frigde ɗinta ta fiddo mata ruwa "Sha ruwa bari na samu na ɗora mana wani abu ko? Sannu. Ki sake jikinki a nan babu mai takura miki in shaa Allahu kin ji?" Kai ta gyaɗa tana yaƙe dai, bayan ta sha ruwan ta fita zuwa kicin na tsakar gida don kamawa Auntyn nata aikin da take yi Dukda ta ƙi tace ta je huta amma sai da ta saka mata hannun suka shiga yi tare tare har suka gama, shinkafa fara da Miyar jajjage da tayi ta saka mata a filet "ɗauka ki koma ƙasan mangoron chan ki shimfida taburma sai ki ci" Yadda ta ce haka tayi Auntyn ta kawo mata ruwa again tuni ta yi nisa a cin abincin. Aunty zainabu dai na ta kokarin haɗa na mijinta don ta san yana gab da shigowa shima cin abincin ranan, dama daga ita sai shi ne gidan Dukda ta fi shekaru goma da aure sai dai har yanzu bata haihu ba, ya sake aure bayan ita amma ba gida daya suke da matar ba itama dai har yanzu babu wani labari na haihuwa kam suna kuma zaman lafiya sossai. Tana ƙoƙarin kai loma yana sallama, ta amsa ya ɗan yi turus yana kallonta gabanta ne ya ɗan faɗi don ganin fuskanshi ya ɗan sauya ko da ta gaishe shi da kalma ɗaya ya amsa kan ya nufi ciki yana kiran zainabu... 🖤Gureenjoh🖤 HAIHUWA DA HANJI (A True life story) Fatima Muhammad Gurin (Gureenjoh) Wattpad-Gureenjo6763 Arewabooks-Gureenjoh *FREE BOOK* *Ba lallai ku ji ni anjima chan ba saboda wani uzuri na so pls bear with me ku riƙe wannan as na chan anjima ɗin tunda Its already friday.* *004* A wurin ta cigaba da zama jiki a saɓule har dai Aunty zainabu ta fito tana kallon fuskanta da har ya ɗuri ruwa saboda ƙuna daga gefe zuwa ƙasan idanunta, Allah ya taƙaita ma bai taɓa idanun ba ta ce "Har kin gama ci Afeefah?" "Eh Aunty na gama" Ta faɗa a hankali don yanayin Auntyn bai mata yadda suka dawo ba idanunta kaman ta yi kuka. "Bari na ba uncle ɗinki abincinshi sai na zo mu tafi gidan mai mazari ya duba miki wannan ƙunar kar ya zama miki damuwa" Daga haka ta yi kitchen, Afeefah ta miƙe ta shiga parlor zuwa ɗakin da ta ajiye mata kayanta daidai ta sauya hijabi zata fito ta ji mijin Auntyn nata murya a sama yana magana "Babu inda za ki da ita zainabu idan ba mayar da ita inda kika ɗauko ta za kiyi ba" Itama Auntyn a sama ta amsa shi "sai dai kuma idan za mu bar maka gidan tare da ita Usman" "Zainabu...!" Da mamaki ya ƙira sunan don a zamansu ba zai ce ga sadda ta ɗaga mishi murya ba sai yau. Kuka ta fara "Haba Usman na fa faɗa maka maganan nan a wurina bashi da matsuguni, Afeefah ɗiyar yayata ce daidai take da tawa wacce zan iya haifa a cikina tana cikin matsi da takurar rayuwa ina tsoron nima Allah ya kama ni a kan banzatar da rayuwarta don Allah ka kalleta da kyau ka ga depression na neman kasheta tun a kananun shekaru..." Ya katse ta "Zainabu ba wai 'yar uwarki na tsana ba ina tsoro ne, ina tsoron abin da zai je ya zo daga nan Anchau har Dutsen-wai babu wanda bai san da labarin yarinyar nan ba, ko kwanan nan ta ci kurwar wani matashi a kasuwa kowa tsoron hulda da ita ya ke sai ni zaki ɗauko ta ki kawo min cikin gida?" Tana kuka sossai tace "Wallahi duk babu gaskiya a lamarin mutane Allah ba zan taɓa yarda Afeefah zata yi maita ba, babu mai mutuwa sai wadda kwanakin shi suka ƙare idan ko don ka zauna da mutum kwana ya ƙare ka zama maye ne da dukkan mu nan Mayu ne don idan baka rasa iyaye ba ma ka rasa makusanta. Idan dai har Afeefah zata bar gidan nan zan bita mu tafi tare ba zan iya sake mayar da ita gidan labaran ba wallahi" Numfashi mai karfi ya sauƙe "shikenan zainabu ai sai ta zauna, amma duk abin da ya je ya zo babu ruwana" "Babu ma abin da zai faru sai alkhairi" A lokacin Afeefah ta sulale ta maƙale jikin gini kamar kadangaruwa ta chusa kanta cikin kafafunta, bata ga laifin mijin Aunty zainabu ba rayuwarsu yake karewa da ya wajaba a kanshi amma Meyasa ita ta zama Mayya? Taya aka yi ta zama Mayya? Amsar da ta kasa ba kanta kenan har yau bata ma san Shigowar Aunty zainabu ba sai dafa ta da tayi ta ji, ta ɗago kai "Aunty don Allah ki yi haƙuri ki mayar da ni gidan kawu zan cigaba da juriya ni karan kaina hankalina ba'a kwance yake ba, tsoro nake ji ina tsananin tsoron kar wani abu ya same ki ta dalilina ba zan iya yafe wa kaina ba..." Kuka ne ya ci karfinta Auntyn ta share mata hawaye "bawa baya taɓa wuce ƙaddarar shi Afeefah babu wanda ke da ran wani a hannunshi face ubangiji don Allah ki kwantar da hankalinki kin ji? Ba zan taɓa iya sake barinki ki zauna wurin 'yan uwan mahaifinki ba muddin ina numfashi. Tashi mu je" Tashi tayi suka fice daga gidan suka je aka saka mata maganin ƙuna a wurin kan suka dawo. Washegari suka sake fita dayake Aunty zainabu yar kasuwa ce tana saya da sayarwa sossai babu wanda bai santa ba a unguwar da ma unguwannin da suke maƙotaka tana saya kuma ta sayar, hatta kayan jikinta in zaki ce kina so ta kan iya cirewa ta sayar miki haka take bata zauna ba, shiyasa take da rufin asirinta a karan kanta makaranta suka je aka yi wa Afeefah interview da kyar aka barta a js2 duk da shekarunta sun wuce ajin, private ce da bai wuci dubu shidda ba termly don haka Aunty ta karbi sample na uniform suka tafi kasuwa ta yanka mata yadi aka ba tela akan zai ɗinka kan su gama sayayya, sayayya sossai ta yi mata da saida tayi ta zub da hawaye tana da sauran gata ashe bata sani ba soyayyar Aunty zainabu ya shige ta tamkar yadda zata so mahaifiyarta. Da kaya sossai suka dawo niki niki, a ɗakin Aunty zainabu inda Afeefahn take suka ya da zango nan ta sake shirya mata kayanta dama ta cire nata masu ɗan dama suka tafi da su kasuwa aka rarrage mata yadda zai ƙarbe ta duk na gidan kawu zubarwa tayi. Rayuwa ne mai cike da natsuwa da kwanciyar hankali ta shiga gudanarwa gidan Aunty zee da uncle usman, tun yana tsoro har ya sake barin ma da ya ga Afeefar yarinya ce mai kwazo, natsuwa da hankali ga ibada da son karatu boko da arabi komai na gidan yanzu ita ke yi don babu wani yawa bata bari Auntyn nata tayi komai muddin tana nan, haka a makaranta malamai sai yabawa kwazonta suke don tana da ilimi kuma akwai saka kai, suna ganin ma a karshen shekara za'a iya bari tayi Junior waec ta tafi ss1 in dai aka tafi a yadda take a yanzu, haka islamiyya tana kokari sossai kusan kowa ya san ta a unguwar saboda yadda Aunty zee ɗin ke nuna ta matsayin ɗiyarta. Sauri sauri ta gama shiri don ta so makara ta fito goye da school bag ɗinta, fuskanta ya fito fess a cikin sky blue hijabin makarantar kyaunta ya sake bayyana na ainihin Black beauty, skin ɗinta har wani sheki yake na samun natsuwa, fararen idanunta take warawa ta inda za ta hango Aunty zee sai dai bata ganta ba, a parlorn ta tsaya ko zata fito daga ɗakin uncle usman ta samu ta mata sallama sai shi ta ga ya fito ta ɗan duka ta gaishe shi ya amsa cikin natsuwa "Dama uncle ina son yin sallama da Auntina ne ko ta koma bacci?" "Eh ai tun da ta fito ta ga kin kamalla komai tana komawa ta sake bingirewa da bacci" Afeefah tayi murmushi "Toh shikenan na wuce makaranta" "karɓi" Ta matsa ta karɓi ɗari biyu da yake miƙa mata "Sai kin dawo a mayar da hankali" Ta amsa tana ficewa da murmushi fal fuskarta kaman ba Afeefar da ba da take yawo da tsananin damuwa da hawaye a ko da yaushe. Ko a makaranta natsuwarta bai kau ba, sam ba zaka ganta tana wasa ba koyaushe littafi na hannunta tana dubawa har ta fara presenting abubuwa a assembly da participating a wasu programs na makarantar, bata da ƙawa har yanzu don duk ajinsu ba sa'annin ta shirin exams ake don haka yau revision ƙarfe sha biyu suka tashi ta nufo gida cikin natsuwa. Sai dai ta samu babu kowa, ta karɓi key a maƙota ta shiga sai da ta zare uniform ɗinta ta sauya da wasu kananun kaya wando ne da dogon riga da ya zo mata har gwiwa kan ta ɗaura dankwalin ta fita zuwa kicin, abinci ta ɗora musu tana mamakin inda Aunty zee ta tafi don bata ce mata za ta fita yau ba kuma kila wani abu ne dai ya taso a chan cikin dangi, ita dai ta san suna da dangin nesa nesa ta ɓangaren mahaifiyarta amma su ma ba wani karbarta suka yi ba ko daukar ta da muhimmanci Dukda ita kanta Aunty zee ɗin ba ta su take ba abinda ke gabanta ma ya fi karfinta. Tana sauƙe faten doyar sai ga su sun shigo "wannan kamshi haka me ake dafa mana ne Afeefah?" Aunty zee ta leƙo kicin ɗin tana tambaya Dariya Afeefah tayi "Aunty faten doya ne fa, amma ya Naji muryarki kaman ta marasa lafiya?" Tana zama a kujeran tsuguno ta janyo filet ta miƙawa Afeefahn, Afeefah ta karɓa ta shiga saka mata kan tace "Eh Afeefah ban jin daaɗi ki taya ni murna kin kusa samun kanwa ko ƙani" Wani irin zaro ido Afeefah tayi kan ta saki ihu tana rungume Aunty zee ɗin sai ta hau hawayen murna, zuciyarta tamkar takarda haka take jinta oh ashe Aunty zee na da rabon ganin 'ya'yanta a duniya? Ita Aunty zee ture ta tayi tana share mata hawaye tace "duk na murnar ne? Yanzu na gama share wa uncle ɗinki da ma ɗayar Auntyn taki da suka tasa ni gaba suna kukan farin ciki shine kema za ki fara? Oya ni sa min abinci in ci cikina kaman ana yasa" Tana murmushi ta ƙarasa saka mata ta dauka mata zuwa gindin bishiyar dake ba da iska mai ni'ima, taburma ta shimfida mata kan ta ajiye mata abincin taje ta kawo mata ruwa tuni ta yi nisa a cin abincinta. Dukda karatu da Afeefah ta saka a gaba saboda tana son fitowa da sakamako mai kyau a term ɗin don Aunty tayi alfahari da ita hakan bai hana ta jajirce wurin kulawa da Aunty zee ɗin ba, ko tsinke in ta ga zata ɗaga za ta karɓe duk abin da take so ko a hira tayi maganan Afeefah za ta yi kokari wurin ganin ta dafa mata shi tunda uncle usman bai Gaza da gidan ba ko ta wani ɓangare, kishiyar Aunty zee ɗin ta kan zo sossai tun samuwar cikin itama da ita ake haduwa ana ririta cikin Dukda Afeefah dai jininsu bai wani haɗu da matar ba tunda iyakarsu gaisuwa, ko hira Aunty zee ke yi da Afeefah in dai ta sa matar bata amsawa ita dai Afeefah bata damu ba tunda babu abin da ya haɗa su duk kuma a je a zo bata wuce awanni biyar zuwa goma a gidan so bata damu ba sam. Kaman yadda ta ci buri ranar hutu sai ga Afeefah da position 3rd ta yi murna kwarai, haka ta dawo gidan da farin ciki. A tsaye ta samu Aunty zee tana tattare kayan da Afeefah ta wanke da safen don shigarwa ciki sai ji tayi an rukunkumeta "Aunty ki taya ni murna" Result ɗin ta miƙa mata "Masha Allah, Alhamdulillah yarinyana kai ya fara ja Allah ubangiji ya sa ki fi haka ya dafa miki a dukkan lamuran ki, Allah ya nuna mana ranar da wannan karatu zai anfanemu ina fata za ki yi kokarin ci gaba da tafiya a haka next term mu ga First rubuce wannan wuri" Kai ta gyaɗa tana ta dariya. **** Aunty zee ce zaune tana ta aikin kallon Afeefah dake yi musu alele don yau da sha'awar shi ta tashi hakan ya sa tana furta wa Afeefah ta hau yi, tana aikin cike da tsafta tana kuma jefawa Aunty zee ɗin hira kaɗan kadan da ya shafi islamiyya da kuma boko da suka koma sati huɗu kenan. A ranta take raya abubuwa dayawa game da Afeefah ɗin tana da matuƙar buri a kan rayuwar Afeefah yadda take very jovial bata fata nan gaba ko ma menene ya karya ta, tana adu'a yadda ta samu farin ciki ta dawwama a haka haske ya cigaba da bibiyar rayuwarta, bata san me gaba ya tanadar ba amma tana mafarkin ganin Afeefah a kololuwar matsayi cike da kwanciyar hankali, danne tunaninta da ya so juyewa ta yi tana cewa Afeefah "Wai kuwa kin san kamanninki har ya ɓaci da Yaya Aisha?" Afeefah ta ɗago ta kalleta yau ne karo na farko da maganar mahaifiyarta ya fito daga bakin Aunty zee ɗin "Na zaci da babana nake kama don mutane kan ce ina kama da inno(kakarta da ta rasu)" Miƙewa Aunty zee ta yi ta shiga ɗaki ta ɗan jima sossai kan ta fito da wasu hotuna hannunta, a lokacin Afeefah ta koma kan taburma ta zauna ta bar alelen ya dafu gefenta Aunty zee da cikinta har ya turo sossai ta zauna. "Jini ne kawai tsakanin ki da inno amma kamanninki tsaff Yaya Aisha ne, kin ganta nan lokacin bikinta ne da babanki" Karo na farko kenan da zata ga mahaifiyarta sai ta ji zuciyarta ya cika da rauni, hannunta na ɗan rawa ta sanya ta karɓa hotunan da ne Black and White matar da ta kasance mahaifiyarta da bata sani ba zaune sanye da zani da riga tare da Ali goggoro, hawayenta ne suka tsinke ganin yadda matar ta zauna tamkar ta kirata ta amsa, da gaske hatta yatsun hannu da na kafar ta irin na mamanta ne, baƙin fatarsu mai sheƙi, manyan fararen idanunsu, tsinin hancin su, karamin bakinsu da fararen hakwaransu hatta dimple guda ɗaya da maman nata ke dashi a gefen hagu itama tana da shi. Raɗaɗin maraici ne ya mamaye zuciyarta, in ba mutuwa ta zama dole ba wa zai so maraici? Maraici ma irin nata marar gata da tushe? Maganganun mutane a kan iyayenta take tunawa sai taji kaman yanzu ne ake jefanta mugayen kalamai, tsintuwa da hantara a kan waenda duk duniya idan da za'a ce me take buƙata ayi mata ko da abu na ƙarshe ne za ta zaɓi su yi rayuwa na har abada amma ake mata Ƙazafin kashe su, anya zuciyarta za ta taɓa warkewa? Anya za ta iya yafewa masu alhakinta? Ɗago raunannun idanunta tayi ta Kalli Aunty zee "Aunty don Allah yaya maita yake? Ya ake yi? Yaya mutanen su ke? Kila baka sanin sadda kake yi in ba hakan ba ta ya zan zaɓi wannan rayuwa akan iyayena? Kila ko cikin fitan hayyacine ake yi ko? Menene ribar yin? Suna yin kuɗi ko Aunty? To me yasa ni ban yi ba? Yanzu wannan pure soul ɗin ni na kasheta ko?" Duk ta rikice ta rasa me zata ce, kalaman suna zuwar mata ne kawai ba tare da ta san fitan su ba, kuka ne ya kufce mata, kukan da ke fita daga ƙasan zuciyarta na ciwo da raɗaɗi... 🖤Gureenjoh🖤 HAIHUWA DA HANJI (A True life story) Fatima Muhammad Gurin (Gureenjoh) Wattpad-Gureenjo6763 Arewabooks-Gureenjoh *FREE BOOK* *Ku yi ta Adu'a mu ƙare a haka ina jin karsashin typing, ina jin daaɗin comments ɗin ku Allah ya bar ƙauna* *005* Hannunta ta riƙe cike da tarin tausayinta da kuma ƙaunar da take jin tana mata fiye da ƙima ta shiga cewa "Na san ba ki kashe kowa ba Afeefah, ƙage ne kawai da Ƙazafi irin da jahilai daga cikin al'ummar mu, ƙarancin ilimi yayi yawa ta yadda mutane suke kasa yarda komai daga Allah ne, a ƙarƙarorin mu ne musamman wanda babu addini sossai za ki samu ko tuntuɓe bawa yayi sai an faɗi dalili da silar shi basu yarda cewa komai Allah ne yake yi ba. Afeefah Kowacce rayuwa akwai ƙalubale ciki ke kuma ta ki kalar ƙalubalen kenan, amma fa na faɗa na sake kar ki saka hakan a ranki saboda babu mai kashewa da raya wa sai ubangiji, duk kuma wanda kika ga ya rasa ransa tabbas lokacin shi ya riga ya ƙare ne ko da sanadi ko babu dole babu maƙawa sai ya tafi, tsakanin ki da su Adu'a ne shine zai ba su tabbacin irin ƙaunar da kike musu. Afeefah mahaifiyarki ba za ta so ta ga kina zub da hawaye ko kin ƙuntatawa kan ki saboda ƙaddarar da ba ke kika ɗorawa kan ki ba, kaman kowace uwa ni ma zan baki shawara ki saka zuciyarki gaba, ki yi Adu'a ki kuma jajirce ki zama tamkar bishiyar gamji sara ko sassaƙa ba su isa su hana ki toho ba" Jikin Aunty zee kawai ta faɗa tana shesheka da kyar ta lallasheta ta bar kukan kan ta ɗago "Na miki alƙawari in shaa Allahu Aunty za ki yi alfahari da ni nan gaba, ba za ki taɓa kuka a kaina ba" "Allah ya amince hajiya ta" Dariya Afeefah ta saki jin ta kirata hajiyarta wadda babban burinta kenan ta zama shahararriyar 'yar kasuwa don tana so tayi kuɗi saboda wani dalili nata. Ƙaurin kamawar leda da suka ji ya sa ta tashi da gudu taje ta sauke tukunyar alelenta daga kan gano tana furta "Aunty alele na so yayi mana buƙulu" Aunty zee na dariya tace "Hira ta yi daaɗi ba, duba ki ga Allah ya sa bata yi komai ba" Sun ci sa'a bata yi komai ba sai na ƙasan guda biyu da ledar ya ƙone nan ta zuba musu tare da Auntyn ta zuba na uncle a kula suka zauna suka ci tare suna hirar su gwanin sha'awa bayan sun gama ita ta yi wanke wanke, ko da ta dawo kan taburman hoton Aunty zee ta bata "Gashi na bar miki, ki ajiye a wurinki" Murmushi ta saki kan ta karɓa tana godiya. Wasa wasa cikin Aunty zee ya shiga watan haihuwa, ta ɓangaren Afeefah tana nan tana ƙoƙarin karatu ka'in da na'in don 2nd term da suka koma ita ta ɗauki na ɗaya kuma 3rd term nan suna ƙare ta tare da ita za'a zana Junior waec ta tafi ss1, a yanzu hatta turanci ya zauna a bakinta ba kaman baya ba da bata wani jin komai, duk wani sayayyar haihuwa tare suke zuwa saboda a hankali ciki ya sa Aunty zee ɗin ta shigar da Afeefah cikin business ɗin ta, wani lokacin ta kan aike ta ita kaɗai ma kasuwa wurin customers ɗinta kuma ta zo ta raba wa clients ɗinta kayan, asusu Aunty zee ta yi mata ta kan ware ladar ta na kasuwanci ta saka mata ciki duk da Afeefah ta nuna ita bata so, tufafi, karatu da kuma cima sau uku da ake bata ya wadatar da ita. Amma Aunty zee ta nuna hakan shine adalci kuma ko nan gaba zata iya anfani da kayanta idan buƙatar hakan ta taso. A yau Aunty zee take cika wata tara da kwana tara kuma a ranar ta kwana da labour mai zafi, hankali tashe da asuba suka tarkata asibiti har da kishiyarta da ta zo ta kwanan musu kasancewar tun da abin ya fara mijin ya ƙirata, ta fi kowa shiga damuwa an ƙarbe ta zuwa ɗakin haihuwa sai jiran abin da hali zai yi, duk Afeefah ta fi ruɗewa babu abin da take tunawa vividly sai irin wahalar nakudar da innarta tayi ƙarshe daga ita har babyn suka koma wannan abu ba zata taɓa mantawa ba, duk kuma ta ga mai ciki sai hantar cikinta ya kaɗa a yanzu Allah kaɗai ya san halin da take ciki na tsoro da fargaba duk adu'ar da ta zo Bakinta ita take yi. Sai Azahar Allah ya taimakesu midwifes ɗin da suka karɓi haihuwar suka fito suna musu albishir na ta samu 'yan biyu mace da namiji faɗin kalar murnar da suka yi ɓata baki ne. Karo na barkatai kenan da Afeefah ta ke kai idanunta kan yaran hakwaranta duk waje, yaran gwanin sha'awa kaman ta Haɗiye su, sam bata san Aunty zee ta farka ba sai ji ta yi tana furta "Suna ba ki sha'awa ko Afeefah?" Da sauri ta juyo tana dariya "Sossai ma Aunty zee, sannu kin farka? Ya jikin?" Ta ɗan saki murmushi. "Masha Allah, jiki Alhamdulillah" Ta furta hawaye na gangaro mata Dukda tana sauƙa sai da ta ji ɗuminsu kan wannan wahalallen baccin ya yi awon gaba da ita amma yanzu da ta farka sai take ganin kaman mafarki, kaman ba'a gaske ba ita ce yau da shekaru arba'in da biyu a duniya kan Allah ya nufe ta da ganin ƙwanta? Har biyu kyautar Allah? Bata san wani irin godiya za ta yiwa mahallicinta ba don ko yau ta faɗi ta mutu ta san ta bar bayan da za su iya tunawa da ita su yi mata Adu'a, bata san daaɗin haihuwar ya kai har haka ba a ganinsu da take kawai ji take kaman ta rabu da baƙin ciki har abada matukar suna kusa da ita. A hankali Afeefah take kokarin ɗaukar su ta kaiwa uwar, daidai shigowan kishiyar Auntyn "A'a Afeefah me haka? Sabbin haihuwan kike ɗaga su anyhow? Wa kika tambaya da za ki ɗaga su?" Yadda take maganan zaka zata wani gagarumin abu Afeefar ta aikata don har ta tsorata, da ta kurawa matar idanu sai ta fahimci kaman akwai dalilin maganar nata amma bata wani mai da hankali ba don Aunty zee ta amsa mata "A'a hamdiyya ai Afeefah ba yarinya ba ce da zata kada yaran baki san ko yanzu ta yi aure zata iya haihuwa ba? Getting to 18yrs ba wasa ba" "kin ga Aunty sabbin haihuwa ne kuma ji da abin mu muke ko kuda bama so ya taɓa su bare wasu da idonsu idon sabon jini su ke Sha'awa" Da sauri Afeefah ta mayar da idanunta kan matar, Aunty zee ma ta ɗago ta kalleta "Me kike nufi Hamdiyya?" "Gaskiya nake faɗa Aunty, hanyar lafiya sai a bi ta da shekara ba za mu so farin cikinmu ya koma baƙin ciki ba" Hawaye ne ke kokarin zubowa Afeefah da jikinta yayi wani irin sanyi, bata ankara ba sai ji ta yi Aunty zee ta ɗora mata yaran duk biyu a kan kafafunta "Afeefah ga su nan ƙannenki ne, ki riƙe su yadda kike so" Juyawa ta yi ga hamdiyya "A kan Afeefah za mu iya samun matsala da ke, ba zan taɓa zuba ido ki tozarta ɗiyata a gabana ba, kin ga yau na haife su ko? Kuma na san daaɗin su ko? To wallahi zan iya zaɓar Afeefah sau dubu kan in zaɓe su sau ɗaya. Ki kiyaye kan mu yi uwar watsi da ke a kan 'yata" "Aunty ni kike yi wa gori a kan wannan mayyar?" Ko kan Aunty zee ta yi magana Uncle ya shigo, kafin ya tambayi me ya faru Hamdiyya ta fashe da kuka mai ƙarfi tana yunƙurin fita, da sauri uncle ya tare ta don shi mutum ne da baya son abin da zai kawo mishi matsala da iyalanshi, yayi kokari ƙwarai wurin haɗe kawunansu ba zai so ko ma menene ya raba su ba, ban da ma yanzu da suka soma tara zuri'a suke kuma cikin farin ciki tsantsa. "Me ya faru hamdiyya? Zainab me ya haɗa ku?" Aunty zee dai komawa ta yi ta zauna sai hamdiyya ce ta kara karfin kukanta "Ka yi haƙuri ni ce da laifi na zaci da ni da Aunty duk ɗaya mu ke kuma 'ya'yanta za su iya zama nawa amma ashe na yi kuskure, in shaa Allah ba zan sake ba" "Zainab!" Uncle ya furta sunan cikin rashin jin daaɗi "Gori kika yi mata?" "Amma dai ka fi kowa sanin hali na Usman, ban yi mata gori ba kuma ba zan taɓa yi mata ba don nima babu wayo na bare dabara ta Allah ya ba ni, abin da take shirin shigowa da shi ne ba zan lamunta ba sam" Hannunshi dake cikin nata hamdiyya ta janye "jita-jita bai taɓa wanzuwa ba matukar babu kamshin gaskiya, an sha tare ni ana gargadina a kan Afeefah amma na ɗauke kai saboda ganin yadda Aunty zee ke ƙaunarta, abin da nake tsoro an ce suna kaunar sababbin jini to don na ce Afeefar ta yi haƙuri da daukar su har su yi kwari shikenan na yi laifi...? Ku yi haƙuri bari na je gida" Tana kai nan ta fice uncle bai ce komai ba don shima karo na ba adadi an tare shi an faɗa mishi abubuwa dayawa kan Afeefah amma baya bari ya shige shi, sai dai kuma bai ji daaɗin reaction na zainab ba da sai a bi abin a hankali tunda dai already akwai maganganu kan Afeefar. "Amma ba ki kyauta ba zainab, na sani kina kaunar Afeefah kasancewar ta marainiya kuma abin tausayi amma kuma sai ki duba kokarin hamdiyya wurin ganin ta bai wa jininki kariya, tun fa jiya tana tare da ke ko runtsawa bata yi ba, ko da kika sauka kika fara bacci haka ta koma gida ta dafo miki ruwan zafi ta biya ta sayo kayan tea saboda kar ki tashi da yunwa babu abunda zai taimaka miki, ai gyara kayanka baya zama sauƙe mu raba" Yana kai nan ya juya ya fice. Idanunta ta mayar kan Afeefah dake hawaye sossai, rabon da taji raɗaɗin zuciya tun ranar da uncle ya amince ta zauna da su sai yau. Yanzu ko da tana cin naman mutum wani bala'in ne da rashin tausayi haɗe da rashin imani zai sa ta ci naman waennan talikan da isowarsu duniya kenan? Me zai sa ta cutar da 'ya'yan wacce ta rungumeta ta cicciɓota ta zaro ta daga cikin bala'i da ƙuncin rayuwa? "Afeefah..." Auntyn ta ƙira sunanta a hankali sai kuma ta kasa magana duk suka yi shiru tsawon lokaci kan nurses suka shigo, hakan ya tilastawa Afeefah barin ɗakin kai tsaye fita tayi daga asibiti ta tsare abin hawa ta faɗa mishi inda za ta, gidan Hamdiyya ta nufa don ta tabbatar a chan za ta samu Uncle usman da ma ita karan kanta hamdiyyar. Hasashenta ya tabbata don kuwa ta same shi tare da hamdiyyar yana ta kokarin bata baki tana tuburewa, maganganu take gayamishi cikin ɗaci da nuna kaman shi ne ai ya zaɓi ya ba Zainabun ciki har ta haifi 'yan biyu tana mata gori. "Haba hamdiyya kema kin san da mutum shi ke ba kanshi haihuwa da yanzu mun tara yaran da bakya zato saboda Zainab macece mai kaunar yara, tun aurenmu na shekara duk inda taji magani muddin bai saba shari'a ba nema take amma da Allah bai turo ba ba gashi yanzu ta haihun ba? Ba'a cire rai daga rahamar ubangiji kema kuma ya san dalilin da ya jinkirta naki namu Adu'a ne kawai da neman zabin alkhairi daga rabbissamawati". "A'a Usman ai ka fi ƙaunar Zainabun idan da Zainabun ta haihu tun farkon aurenku da baka auro ni ba, silar rashin haihuwar ne ta saka ka kara aure ba don kana so na ba kuma ta haihun ai..." sallamar ta ya katse musu maganar duk suka mayar da hankali kanta. 🖤Gureenjoh🖤 HAIHUWA DA HANJI (A True life story) Fatima Muhammad Gurin (Gureenjoh) Wattpad-Gureenjo6763 Arewabooks-Gureenjoh *FREE BOOK* *006* "Uncle, Aunty hamdiyya don Allah ku yi haƙuri, ban zo da niyyar wargaza zaman ku ba, na sani Auntyna ta faɗa miki magana ne saboda irin ƙaunar da take mini amma ni na san gaskiya kika faɗa, don Allah ki koma asibitin ki cigaba da kula da ita da jariran ni zan koma gida zan cigaba da jira har lokacin da ya kamata a ce na ɗauke su ɗin" Cikin wani kalar sanyin murya take maganan, idanunta har lokacin ba su daina zubar da hawaye ba. Uncle ɗin tausayinta ya ji yayinda hamdiyya ta taɓe baki ta ce "Toh ai shikenan, ni ba na yi magana ba ne da wata manufa kawai dai ina kare yaran da yanzu ne muka fara morewa wanzuwar su ba za mu juri dare ɗaya a yi abincin meeting da su ba" Uncle ne ya katse ta "ya isa haka, ki tashi ki koma asibitin. Afeefah tashi mu je in sauƙe ki a babur na" Miƙewa ta yi suka fice daga gidan, har suka iso gidan Auntyn nata magana bai haɗa su ba ta sauƙa ta shige yayinda ya juya ya koma asibitin. Bata bari abin ya cigaba da damunta ba ta kintsa gidan tamkar Auntyn na nan ta ɗora girki marar nauyi ta ci ta zuba saura a kula kan ta ɗan kwanta bacci, har ga Allah ta tsame kanta ne saboda gudun abin da zai je ya dawo sam ba zata so wani ya yi kuka sanadin ta ba bare Auntyn ta don haka tana ganin shawarar da ta yanke shine daidai Sai da Aunty zee ta kara kwana biyu a asibiti saboda postpartum ciwon ciki da ya matsa mata amma duk da haka sai damun uncle usman take akan maganan Afeefar har fushi ta yi ta matsa a sallame ta saboda tunanin ta kar Afeefar ta ji an ware ta ko ta sanyawa kanta damuwa, duk da sun shirya da hamdiyya sai dai har aka yi sallamar hirar arziki bai haɗa su ba don ta matuƙar jin zafin abin da ta yiwa Afeefar. Tana sanya kai cikin gidan ta soma kiran "Afeefah! Afeefah!!" Da gudu Afeefah da ke zaune a parlor tana kallo ta fito ta rungumeta tana murmushin ganinta, Auntyn ta ɗago fuskarta sai ta sauke ajiyar zuciya "Afeefah ni kika yasar a asibiti ko?" "A'a Aunty ban isa yasar da ke ba wallahi, na bari ne Aunty hamdiyya ta kula da ku ni kuma sai in kula da gida ba gashi ba gidan ma ya ji daaɗi, da missing ɗin mu da zai yi sai yayi mishi yawa" Dariya Aunty zee ta yi tana girgiza kai, a parlor suka ya da masauki kan a natsa ma maƙota da abokan arziki an fara shigowa barka tuni gidan ya soma ɗinkewa da jama'a nan Afeefah ta shiga jeka ka dawo. Zamanta da hamdiyya na kwanaki shidda ba karamin wahala ta sha ba ta kuma danne zuciyarta, ko Aunty bata bari ta san hamdiyyar tana matukar musguna mata ba ta yadda ko satan kallon yaran ta yi sai ta yaɓa mata baƙar magana, har tsoron kallonsu take Dukda tana jin son su tamkar jini da tsokarta ta sha ɓuya tayi kuka sossai na mummunar shaidar da take dashi don bata tsira ba ranar suna har nuna ta hamdiyya ta saka ake yi saboda kananun maganganu duk Aunty bata sani ba. Auntyn Ta yi matuƙar kyau cikin milk leshin ta yayinda yaran suke sanye cikin kyawawan tufafinsu pink da blue, Afeefah ma cikin leshin da Auntyn ta yi mata musamman na suna maroon ta shirya ta yi mugun kyau Aunty zee har ajiye ta tayi ta zana mata liner a baki ta saka ta saka kwalli ta shafa mata powder sai tayi kaman ka sace ta ka gudu, masu hidima da kitchen ita suke kira tana miƙawa mutane abinci daidai ta zo miƙawa wasu mata kenan da yake ta bayansu ta zo ta ji ɗayar tana cewa "Ni kam dai ina tausayawa Zainabu saboda fa da gaske yarinyar da take riƙo rikakkiyar Mayya ce kuma fa an ce Mayu sun fi zaluntar wanda ya ji tausayin su" Ɗayar ta ce "Ni fa ban san yarinyar ba amma kuma ina da labarin tun tana ciki take cin maita, uban ta ma bai tsira ba haka uwar da ta haife ta, aiko Allah raba mu da irin wannan iri. Haihuwa bata yi rana ba" Wani irin abu mai nauyi ne ya taso ya tsayawa Afeefah a kirji tana ji na ukunsu na furta "za ki gane ta mana wata baƙa marar kiba ta saka leshi maroon, ai daga kallon idanunta da suke manya kaman kwai kin san za'a ga kurwa da kyau... Allah dai ya hana farin ciki komawa baƙin ciki" Gabansu ta zagayo suka ɗan sha jinin jikinsu ganin fuskarta babu ɗigon walwala idanunta da suka surke zuwa ja ta ɗan zuba musu kan ta ajiye abincin ta juya ta bar wurin. A karshe dai ba'a tashi suna lafiya ba don wata wai aljannunta sun tashi ai sai ta kashe Afeefah Mayya ce! nan fa gidan suna ya kachame dayawa suka shiga kururuwa su ma, da ƙyar aka fita da ita a gidan zuwa maƙota ban da kuka babu abin da take, bata san wani irin tunani zata yi ba duk ta ji kaman ta sallamarwa duniya farin ciki da rayuwarta sai ta tuna Aunty zee da ta yarda da ita take kuma bata kariya don yanzu ma ita ce ta nuna jan ido ta sallami kowa da abin da za'a yi sai ya fi haka, chan kuryar maƙociyarsu ta takure tana kuka sossai bata ji Shigowar Aunty zee ba amma ta ji hannu ya taɓa ta firgita ta yi ta miƙe tsaye tana girgiza kai "Wallahi ni ba Mayya ba ce! Ban san ya ake yi ba don Allah ku yi haƙuri ban taɓa cin naman mutum ba wallahi..!" A rikice take maimaitawa da sauri Aunty zee ta rungumeta tana hawayen tausayinta "Ya isa Afeefah! Ni ce! Auntynki ce, na sani wallahi na sani ke ba Mayya ba ce na yarda da ke" Kuka kawai ta saki mai tsuma zuciya tana yin luff a jikin Aunty zee ɗin. Jiki a sanyaye duk suka dawo gidan, yayinda abin da ya faru a sunan ya tsayawa Afeefar ta yadda ko kuzarin taɓa yaran bata da shi, tsoro take ji kar ta taɓa su abu ya faru haka Aunty zee ta sa uncle usman a gaba tana kuka sossai "Duk laifin matar ka ne usman da bata fara ba da hakan bai faru ba, yaran nan fa kannen Afeefah ne amma ka ga yadda take baya baya da su ko taɓa su sai na yi da gaske take yi! Haba mana ko bata duba komai ba ta duba maraicinta mana wallahi ta ɗauki alhakinta dayawa kuma ni kam ta daina burgeni sam" Shiru yayi chan ya ce "Ki yi haƙuri zan yi mata magana, amma ki dinga dubawa itama hamdiyyar ba don tsanar Afeefah bane ya sa take hakan saboda kare yaran nan ne ganin tsawon lokacin da muka ɗauka kafin Allah ya ba mu" "Wallahi na fi ƙaunarta a kan su, ta cigaba da rayuwa da wannan tsangwamar rayuwarta na cikin haɗari don Allah zan roƙe ka Alfarma don girman Allah kar ka chanza mata kaman yadda ka fara mata, ka dubi maraicinta ka riƙe ta kamar yadda za ka riƙe suhail da suhaila". Hannayenta duk biyu ya riƙe "Ban tsani Afeefah ba Zainabu, in shaa Allahu kuma zan cigaba da iya ƙoƙarina a kanta" "na gode sossai Baban 'yan biyu" Ya saki murmushi ita ma ta mayar masa. Duk su biyun sun mayar da hankali kanta ta yadda hatta shi uncle ɗin kan ja Afeefar jiki ko ma ya bata babies ɗin da take matukar so ta riƙe, yau satinsu na biyu kenan a duniya. Tsaki Aunty zee ta ɗan ja kaɗan karo na ba adadi hakan ya saka Afeefah dake jijjiga suhaila yayinda Auntyn ke ba Suhail Mama ta kalleta ganin tana ta yamutsa fuska ya saka Afeefar katse shirun nasu "Aunty lafiya kuwa?" Ta sake jan wani tsakin karo na barkatai kan ta furta "Wlh Afeefah ciwon ciki ne ke ɗan matsa min tun haihuwar nan kullum sai na yi shi kaman ƙa'ida" "Sannu Allah ya ba ki lafiya, babu maganin da suka ba ki a asibiti?" "Akwai fa ina sha amma kaman bana sha" "Sannu" Haka tayi ta jera mata duk ta saka kanta a damuwa domin sam bata so taji wani na ciwo a gidan sai gabanta yayi ta faɗuwa fargaba ya bi ya rufeta har sai an furta mata yayi sauƙi. Shigowar Uncle da karbar babyn da yayi daga hannunta ya sa ta yi musu sai da safe ta shige ta bar su nan parlor. Chan cikin dare sai ta ji kaman ana motsi da ƙarfi, sai kuma ta ji bugun kofar ɗakinta a razane ta farka tana salati jin Muryar uncle ya sa ta dirko da hanzari ta zo ta buɗe kofar "Afeefah ki zauna da yaran nan idan sun yi kuka ki ba su madara zan kai Auntynki asibiti ciwon ciki ya tasar mata sossai" Tuni ta rikice hawaye har sun fara zarya a idanunta. "Toh uncle" Ta faɗa tana bin bayanshi, shi ya riƙo Aunty zee da ke tafiya da kyar Afeefah na ta bin su tana share hawaye har zuwa kan babur ya hau ta kwanta jikinshi suka fice tana ta jera mata sannu da Allah ya bata lafiya. sai da taje ta rufe kofa kan ta dawo kan yaran ta zabga tagumi cike da damuwar ciwon Auntyn. Yaran sam ba su da rikici daman, tun tana tagumi har bacci ya sure ta a kansu ƙiran Sallar farko da kukan suhaila su ne suka farkar da ita, ta tashi ta haɗa musu NAN1 ɗin su da ake basu saboda abinci ya ishe su, ba zallar nono Auntyn ke ba su ba, sai da ta saisaita ya zama da dumi cikin tsafta ta fara ba su don suhailar na koshi sai suhail ma ya tashi bayan ta gama ta fice taje tayi alwala ta zo ta fara sallah sai da ta idar tayi Adu'a ciki har da roƙon Allah ya ba Auntynta lafiya kan ta miƙe ta bar sallayar zuwa tsakar gida. ƙoƙarin ɗora musu breakfast ta fara a natse take aikin Dukda hankalinta rabi na ga su Uncle da suke asibiti rabi na ga 'yan biyu kar su farka bata ji kukansu ba har ta gama haɗa abinda zata buƙata ta ɗora kan ta shiga sharar tsakar gidan. Ta gama haɗawa tana ƙoƙarin kwashewa kenan ta ji ana bubbuga kofa ba irin bugun hankali ba, jikin kofar ta isa sai ta ji kaman surutai dai ba na mutum ɗaya ba, bata buɗe ba ta shiga tambayar waye ne? "Ki buɗe mana ai za ki gani!" Muryar hamdiyya da ta ji ya sa ta buɗe kofar sai dai me za ta gani...! 🖤Gureenjoh🖤 HAIHUWA DA HANJI (A True life story) Fatima Muhammad Gurin (Gureenjoh) Wattpad-Gureenjo6763 Arewabooks-Gureenjoh *FREE BOOK* *Jama'a kuna manta cewa na rubuta True life story a jikin labarin nan, Meyasa na yi kyauta ne kam? Saboda ina so mu ƙaru da ilimin dake ciki, na tabbatar daga page 1 zuwa yanzu kun zaƙulo darusa masu dumbin yawa kuma ko ban kawo gyara ciki ba kun san amsar hakan. Wallahil azeem ban ƙara komai a labarin Afeefah ba, ban ce babu ƙari ba akwai amma sai a gaba yanzu duk abinda kuka gani a gaske ne ban chanza komai ba, please bear with me🙏* *007* Wasu gungun matasa ne ɗauke da makamai suna ƙoƙarin Hankaɗa hamdiyya su rufta mata ai da wani irin hanzari ta mayar da kofar ta rufe jikinta na wani irin ɗaukar tsuma, hankalinta sai ta ji yayi wani irin tashi tsoro da fargaba suka rufe ta, ko kafafunta ta kasa motsa su daga inda take tsaye... Ƙuuuuu haka cikinta yayi wani irin ƙara a sadda ta ji kukan uncle haɗi da maganarshi daga bakin kofan "Ki buɗe ki ba ni yarana...! Kin riga kin cuce ni kin raba ni da uwarsu rabuwa ta har Abada a yanzu ba zan iya sake ɗaukar raba ni da su ba, in kuma su ma kin cinye kurwarsu ne kaman uwarsu nima duk ki haɗa da ni ki cinye Afeefah..." Sossai yake gunji daga jin muryarshi zaka san baya cikin hayyacinshi ne. Tsurewa ta yi tana jin kaman ta zauce ko kunnuwanta ba sa ji da kyau. Tamkar sauƙar aradu ta ji wani da kaman yanzu ya iso a gigice yana furta "Da gaske ne Usman Zainabu ta rasu?" 'Zainabu ta rasu!' Ko kan kalaman su gama shiga kwakwalwanta sai ji tayi uncle na amsawa "Zainabu ta tafi ta bar ni. Sai da aka gargaɗe ni amma na ƙi saurara saboda ta ba ni yaƙini a kan yarinyar, ashe ba haka ba ne kai duniya...! Ashe wanda ya maka rana za ka iya masa dare? Afeefah ta yi mana shigo shigo ba zurfi, lafiya ƙalau muka kwanta da zainabu daga ciwon ciki farar ɗaya muna zuwa asibiti sai ga kiran hamdiyya take sanar min ta yi mummunar mafarki a kan zainabu, sai na sanar mata muna asibiti bata da lafiya ta tsorata tace gata nan zuwa Dukda dare ne haka ta bi gidan wani malami ta taho da shi akan mafarkinta mai muni ne Afeefah ta gama cinye kayan cikin zainabu ashe da gaske ne! Duk irin taimakon da malamin nan ya so bata ya gaza haka likitoci suna gani ta ce ga garin ku..." Hamdiyya ta chafe cikin kuka "in ba aikin maita ba menene wannan? an riga an cinye mata kurwa, sai da na faɗa wlh sai da na gargadi Aunty akan mayyar yarinyar nan.." Gayyar mutane bayan waenda hamdiyyar ta zo da su suka sake cigaba da taruwa suna hayaniya akan tabbas ita ce mayyar ai dama daga Dutsen-wai ma gudu wa ta yi saboda yunkurin kashe ta da Ƴan uwan wadda ta kashe last suke kawai a kasheta. Ƙafafunta sai suka gaza ɗaukarta, ta zube yaraf a ƙasa, hawayen da suke zuba tuntuni sai suka ƙafe kamar rijiyar da aka yi wa yaso. Zuciyarta na raya mata cewa da gaske ita ɗin annoba ce, da gaske ita ɗin mayya ce. Tana ji jama'a na maimaita lafiya ƙalau ta kwanta ciwon ciki ya turniƙe ta cikin dare daga isa asibitin su sai mutuwa. Hujjar da suka kafa kenan suna ƙara tunzura shi wasu na ta faɗan abubuwan da ita karan kanta da ake yi wa ƙagen bata san yaushe aka yi ba, ina ma da bata biyo Aunty zee ba? Ina ma da bata zo ba! Ina ma da bata biyo ta ba! Da gudu ta miƙe tana komawa cikin ɗaki gunjin wahalallen kukan da ta fashe da shi haɗe da ƙara na bala'i na cika ilahirin gidan ba wai don gudun rayuwarta da mijin antinta ke ta iƙirarin ita ma sai an kasheta ta bi matarsa ba sai don rungumar mutuwar a karan kanta, tana so a yau ta kawo karshen komai tana so tayi mai gabaɗaya da rayuwarta wai haihuwa da hanji... bayi ta shige kai tsaye babu wani tunani ko shawara ta zaro piya-piya da su ke ajiyewa saboda sauro ta buɗe tare da kafa bakinta a kai tana kuka me tsanani da dugunzuma zuciya, ƙwatt! ƙwatt!! ƙwatt!!! haka maƙogoronta ke ba da sauti a sadda ta ke haɗiyewa tana jin ta yi sallama da rayuwa kaman yadda mamanta, babanta, kakar ta, innarta da ma Aunty zee suka yi. Lallai an yi mata mummunan zato da ba za ta taɓa wankuwa ba a duniya, ta gaza! Ta kasa rayuwa kaman kowa, a yanzu wa zai dauke ta kuma? Wa zai yarda wani nasa ya aure ta ko ya raɓe ta? Mutuwa ita ce abu mafi sauƙi a gare ta kaman yadda ta yankewa kanta. Kururuwa da take ji a nesa bai sa ta sauƙe kwalbar fiya-fiyan ba sai da ta ji an yi wani irin wurgi da kwalbar ya tafi ƙasa yana tarwatsewa kwatankwacin yadda rayuwarta ta tarwatse. Dishi Dishi take gani jiri ya diɓeta sai taji an tare ta sun tafi a tare suuuuu ƙasa. *** A kafa su ke takawa sanye cikin uniform kasancewar assignment da aka ba su a cikin Anchau sun gama shi kuma a lokacin ne suke shirin barin garin zuwa cikin Kaduna, Zaratan matasa ne biyu sanye da khakin Sojoji daga yanayin tafiya da tsarin zubin halittarsu zai tabbatar maka da waennan ɗin ko a cikin Sojoji zaƙaƙuran ne, da wani irin ginshira suke tafiyan kowannensu na da kalar nashi kyaun, haiba da tarin kwarjini abin da ya bambamta uniform ɗin nasu abu ɗaya ne, shi wadda ya fi cin maganin fuskan nan tamau daga damtsen hannunshi akwai wani farin bandage da aka zagaye ƙarshen uniform ɗin dashi a jiki akwai zanen plus ➕ Da jan tawada wadda zai tabbatar maka da wannan ɗin Medical soldier ne. "Ko wanchan taron na me?" Na gefen da bai kai haske da wani irin ƙasaitar wanchan ɗin ba ya faɗa cikin natsuwa. A sace ya ɗan kalli wurin ya watsar kaman ba zai yi magana ba cikin halinshi na i don't care ya furta "How would I know Saleem after all tare mu ke da kai?" Wadda aka ƙira da Saleem ya sake kallon taron a lokacin da suka tunkaro su sossai "Ko ma menene Rayyan ba na tunanin lafiya..." Ko ya tanka sai ma kanshi da ya mayar ƙasa yana ci gaba da takunshi cikin ƙasaita da isa kaman yadda yake a halittarsa. Ihu da ƙarar da ya ratsa kunnuwansu haɗe da furta kalaman "sai mun kasheta yau za mu ga karshen maita" Da jama'ar wurin suke ta furta wa wasu ma ɗauke da makamai ya sa Saleem taka birki yana riƙo hannun Rayyan da yayi kaman bai ji ba. "Guy akwai matsala, we cannot neglet our duty ba za mu ga ana shirin ɓarna mu kama hanya mu wuce ba" Ko ya tanka sai birkitattun idanunsa da ya kai wurin yana nazarin situation ɗin fuskar nan babu walwala ko na miskala zarratin. Bai yi magana ba har Saleem ya isa ga mutanen, yana tsaye daga gefe da farko jama'ar sun so yin gardama amma jin ya kira akan a turo squad kuma ya zaro bindiga ya sa aka fara watsewa uncle da hamdiyya dai sai kuka da Allah ya isa suke yi, a mayar da maganan da ake ne ya ji abin da ke faruwa. "Wait here!" Ya faɗawa Saleem kan ya haye katangar gidan da ba shi da wani tsawo chan chan, bai buɗe kofan ba sai yayi cikin gidan yana dube dube, motsi da Sheshekar da ya ji ne ya saka shi kai kyawawan idanunshi wurin sai suka sauƙa kan kwalbar fiya-fiya a take warin ya shige cikin hancin shi da wani kalar hanzari ya fusgo madarar ruwa da ya gani nan cikin ɗakin Auntyn kasancewar ta mai jego ya fasa guda biyu ya isa gabanta ya sanya hannu yayi wani irin wurgi da kwalbar ya haɗe da gini ya tarwatse... Sulalewa take ƙoƙarin yi a lokacin da ya ɗago madarar yana shirin bata, bashi da zaɓin da ya wuce ya sanya hannunshi ɗaya ya tareta suka kai ƙasa ita tana ƙoƙarin sumewa shi kuwa ya sauƙa a kan gwiwowinshi, kanta ya ɗago da take ta kokawar numfashi ya kafa madarar tare da matse hancinta sai da ta kwankwadi mai yawan gaske kan ta sake yunkurowa tayi gaba wani kalar amai na kwace mata, tana gamawa ya sake dura mata ɗayar ta sake kwarara wani aman ko idanunta bata iya buɗewa alamu sun nuna ta jima da ficewa hayyacinta haka ya sanya hannu ya ɗauko ta zuwa waje, Fitowar shi da isowar motar Sojoji lokaci guda sai ciki aka sanya ta ya shiga tare da barin Saleem wurin suka fice a guje kaman yadda suka saba. Da gudu Uncle da hamdiyya suka shiga suka ɗauko yaran da ke ta kuka suna rurrungumesu a lokaci ɗaya suna ta tsinewa Afeefah, Saleem dake tsaye ya iso gangar uncle ɗin "A komai ya kamata ku dinga adalci da tunani, ƙage ko sharri ba abu bane mai kyau shin kun taɓa jin maita ko a addini? Ko kun taɓa ganinta ta yi maitar?" "Wallahi billahi na rantse da Allah idona idon Afeefah sai na sa an kasheta gwara ku gaya mata tun daga inda ta tafi ta san inda dare ya mata, sam Shigowar ta rayuwarmu bai mana rana ba" Hamdiyya ta karɓi zancen "ba kai kaɗai ba ai gwara mata mutuwar ta da dawowa unguwar nan tsinanniya" Juyawa kawai Saleem yayi ya bar gidan suna ta zaginta da kwashe mata albarka wasu mata na shigowa ana ta kokarin mayar da magana ai dama an gargadesu. BAYAN WASU AWANNI A hankali ta shiga ƙoƙarin buɗe idanunta da suka matuƙar yi mata nauyi tana jin yadda kanta yake wani sarawa, a tunanin ta za ta tsinci kanta cikin ƙabari ne kaman yadda ta jima da sallamar da rayuwarta wa mutuwa sai kuma ta ga akasin hakan. Idan ma tunanin ta ya bata daidai kaman nan ɗin ɗakin asibiti ne take ciki duba da yanayin tsarin ɗakin da kuma ƙarin ruwan da ke shiga jikinta ta canular dake ɗaure a hannunta. Tunanin dalilin mutuwar tata ne ya bijiro mata kaman ana haska mata majigin rayuwarta... "Aunty zee ta rasu" Daram! Haka zuciyarta ya buga zuruf ta miƙe zaune kaman ba jiri ne ke walagigi da rayuwarta ba, hannayenta ta sa duk biyu ta toshe dukka kunnuwanta don ji take kaman ana maimaita mata kalaman na rasuwar Aunty zee da speakern da ya fi komai ƙara a duniya. Tamkar zautacciya haka ta saki wani irin ƙara da ya shigo da nurses har uku ɗakin da gudu da ma an ba su aikin kula da ita kar ta farka ta sake yunkurin cutar da rayuwarta. Shigowar su da fara fusge-fusgenta kusan lokaci guda rirriƙeta suke kokarin yi amma kaman mai tashin aljannu sai wani irin ihu take mai tafe da gunjin kuka mai taɓa zuciyar mai saurare don kowa ya ji kukan ya san ba na wasa bane "Ku barni na mutu! Don Allah ku bar ni na mutu ba zan iya rayuwa ba! Ku sakeni....! Ku sake ni na ce!" Duk ta haukace kuma yawan su bai sa sun iya natsar da ita ba.. "Will you shut up and stay still?? Giyar wake kika sha ne?? Hauka kike yi ne??" Kalaman suka fito cikin wani irin amo da ya amsa duka ɗakin... 🖤Gureenjoh🖤 HAIHUWA DA HANJI (A True life story) Fatima Muhammad Gurin (Gureenjoh) Wattpad-Gureenjo6763 Arewabooks-Gureenjoh *FREE BOOK* *008* "Karen hauka ne ya cije ki? Ko stupid lunatic brain naki hauka yake karanto miki?? Are you stupid?? Ki kashe kan naki oya take this..." Muryarshi mai cike da fushi haɗe da zafi ya cigaba da sauƙa wane aradu bisa kan su ba ita kaɗai ba hatta nurses da suka san shi sai da suka sha jinin jikinsu a take, wani irin shiru ne ya ratsa ɗakin kan takun sawayenshi suka amsa ya isa ganganta riƙe da scapel (aska irin ta likitoci) ya damƙa mata a hannu ya fusgo ɗayan da karfi har canular ɗinta na fita daidai jijiyar Wrist ɗinta ya sa yatsarshi babba. "Nan! Nan kawai za ki katse ki mutu idan sha'awar wutan Jahannama ne yake ɗibarki, ba mutuwa kike ƙaunar yi kafura ki tabbata cikin azabar Allah ba? Oya yanke mana!!!" A zaune take amma sai da tayi wani tsallen tsoro saboda tsawar da ya daka mata sai da ya kaɗa 'yar hanjin ta. "Haba Rayyan, yarinya ce don Allah ka bita a hankali mana ka ga yadda duk ka firgitata?" A zafafe yace "Za ta ci kashi ne salim? Muddin ba za ta ci kashi ba to tabbas babu zancen yaranta a lamarin ta sai tsagwaron iskanci da ƙarancin ilimin addini... Tana tunanin da kashe kai shi ne hukunci mafi sauƙi ga bawa a duk sadda ƙaddara ta ruro wutarta za ta samu miliyoyin mutane a raye ne?" Ita dai bata san a wace duniyar take ba don tsabar yadda take kaɗuwa bata sani ba a farke take ko a sume ya juyo da figitattun idanunsa da basu yi mata kala da na mutane ba ya zura mata "To bari ki ji, idan ma ba ki sani ba ki sani idan ma kin sani danne sanin kika yi to gidahumar kwakwalwarki ta tuna kuma ta yi hadda wutar Allah ya fi gaban wasa, kar ki zaci wannan wuta da kuke girki da shi duk zafi da raɗaɗin na wannan duniyar, duk irin hatsarinshi da in ya ɗan taɓa ki za ki ihu sai da aka wanke shi sau dubu saba'in kan aka jefo mana" Kanshi ya dafa yana wani jan tsaki mai tsawo saboda rabon da yayi magana haka ya manta, amma dole ya ƙarasa don zuciyarshi a tunzure take ji yake kaman ya faffalla mata maruka wa ta fi shiga cikin damuwa da zata kashe kanta? "Tabbas duk wanda yana musulmi ya kashe kanshi da gangan ya fita daga musulunci kuma zai mutu ya kuma tashi ranar gobe a kafiri... Ƙarbar kaddara mai kyau ko marar kyau na ɗaya daga biyar ɗin cikacikan musulunci. Ki yi gaggawar tuba domin a yanzu haka kin nunawa ubangiji ba ki da cikakkiyar imani ki kuma gode Allah we were there on time Nonsense…! Wani irin rawa da jikinta yake ya sa tuni askar ya zame ya faɗi ƙasa yana ba da sautin kwankwataraaaan, yadda kalamanshi suke fita a hautsine cike da zafi da ɗaci mai tarin zallar gaskiya haka su ke hautsina mata 'yar hanji suna kaɗa hantarta kuma suna shiganta ba da wasa ba. Tun da idanunta suka sauƙa cikin nashi a karon farko ta yi saurin sadda nata ƙasa don ba za ta iya ko da gangancin jurar ganin cikinsu ba, ganin tana shirin zubewa a sume ya sa salim damke hannun Rayyan da har kaman zai rufeta da duka at any moment ya ce "Calm down please dude" Ya maimaita kusan sau uku don ya san hayaƙin kan rayyan ba kowa ne ke iyawa dashi ba, hatta shi karan kanshi wani lokacin shakkar shi yake saboda wani irin kwarjini da Allah ya zuba masa na ban mamaki, bare wannan yarinya da rubdugun rayuwa yayi mata ƙatutu. "Sister ku taimaka mata ko da allurar bacci ne samu ta huta ta kuma samu natsuwa please" Salim ɗin yayi directing kalaman to nurses ɗin, da sauri suka shiga ƙoƙarin aiwatarwa don babu wadda bai san Zafin kan Surgeon General Ryan Moh'd Khamis ba, a lokacin da suka roƙi ta kwanta ko uhmm bata yi ba ta miƙe flat zuciyarta har a lokacin tana jin shi a tsaye kyamm tsabar tsoro. Jan Rayyan da ke tsaye ya zubawa gini idanu yayi suka fice, haɗadɗen office ne mai cike da ƙawa tamkar ba asibiti ba suka shiga, fasalta kyau da tsaruwar office ɗin bata lokaci ne sai wani masifaffen ƙamshi yake fitarwa tare da sanyin Ac mai ratsa jiki. A doguwar kujera Brown mai cin mutum uku salim ya mishi masauki, ya nufi chan dungu wurin wani tsararren frigde ya buɗe ya ɗauko mishi ruwa masu sanyi ya taho ya miƙa mishi bayan ya ɓalle murfin ba tare da yayi magana ba ya karɓa kaman faɗa ya kafa kai, sai da ya shanye tasss kan yayi wurgi da goran "I need some space Salim" Maganan ya fito daga chan ƙasan maƙogoronshi in ba ma salim ɗin hankalinshi na kanshi ba ba zai taɓa cewa shine yayi maganan ba, dama kuma ya san za'a yi hakan dole ya fice ya barshi nan yana zamewa kwance cikin kujerar Dukda tsawon shi ya zartawa kujeran nesa ba kusa ba. Salim na fita ɗakin ya koma ya janyo kujera ya zauna tare da tsura mata idanu, duk da ba zai ƙira ta kyakyawa ajin farko ba sai dai tana da nata qualities ɗin na daban da ba kowa ke da shi ba kuma da matuƙar wuya a same su wurin wata macen, baƙa ce amma baƙin mai haske tana da doguwar tsiririn fuska da dogon hanci duk da idanunta ya musu kallo ne na tausayi don a rine suke a kuma firgice zai iya ƙiransu manya kuma farare, girarta kaman ita ta zana yanayin tsawon gashin idanunta da ma masu sheƙi irin na baƙaken Fulani dake kwance lublub bisa goshinta za su tabbatar maka da cewa tana da tarin suman kai, bakinta kalar peach da ya ƙara haskaka kalar skin ɗinta ya amshi fuskartata. Ta yi mishi yarinya kwarai da tunanin kisan kai, kuma ya tabbatar duk abin da zai saka mutum tunanin kashe kan shi ba ƙarami ba, ba zai ce ga iya adadin lokutan da ya ɗauka yana gwamutsa biyar da goma ba a kan matsalar yarinyar sai motsin ta ya ji, da ɗan hanzari ya mayar da hankalinshi kanta don dama tuntuni kallonshi na a gareta. "Sannu 'yanmata kin farka?" Tsura mishi idanu ta yi tana tariyo abin da ya faru a ɗazu da sauri ta shiga dube dube tana jin gudun zuciyarta na wani irin ƙaruwa ganin firgici a idanunta ya sa ya miƙe ya isa gangarta yana furta "Natsu 'yanmata dodon ɗazu ba ya nan, da ma matuƙar wuya ki sake ganinshi a gangarki." Numfashi mai nauyi ta sauƙe duk da tarin tsoron da take ciki hakan bai hana kalamanshi na ɗazu na sake bijiro mata ba, wani irin sanyin jiki da tsoron Allah na lulluɓeta a take ta fara tuba hawayenta na ɓallewa take furta "Allah na tuba ya Allah! Wallahi na yi nadama Allah na san kana sane dani da kuma halin da nake ciki ya Allah ka sassauta min, Allah ka ba ni ikon ƙarbar kaddara ta a yadda ta zo min Allah ka yafe min..." Sossai take kuka har tana shiɗewa, bai hana ta ba ya barta tayi kukan sossai har tana ajiyar zuciya kan ya ɗauki ruwa ya miƙa mata, sai da ta jima tana kallon hannun nashi kan ta sanya hannu ta karɓa ta sha sossai kan ta sauƙar tare da gintsewa cikin hannunta tana sauƙe numfashi ta sake ƙura wa bango idanu. "Ya Sunanki?" Ta ji tambayar ya zo mata, kallonshi ta yi yana da tausayi haka yana da sanyin hali duk da khakin sojojin da ta ganshi da shi ba irin wanchan ɗayan ba da ko a mafarki bata fata ta sake ganinshi don kila sai ta sume. "Afeefah" Ta furta a hankali "kina da suna mai daaɗi Afeefah". Shiru ta yi. "Ko za ki kwanta ki huta? Ko in samo miki abin da za ki ci?" Nan ma shiru tayi, a hankali kuma ko me ta tuna tace "Eh" "Eh wa wanne kenan? Kwanciya ko abinci?" Da wasa yayi maganan hakan ya sa ta sake kallonshi kan tace "kwanciya" "duk biyu dai Afeefah, yanzu kwanta ki na hutawa ni kuma zan je in samo miki abincin kin ga ina dawowa ke kuma kin gama hutawa sai cin abinci ko?" Ta gyaɗa kai "yauwa Afeefah" Kwanciya tayi shi kuma ya fice. Ya fi awa ɗaya da fita kan ya dawo, ya samu wani baccin ya ɗauke ta yadda kuma fuskanta da idanunta suka sake suntuma suka tabbatar mishi da ta sake wani kukan fiye ma da na ɗazu. Sossai ta bashi tausayi adu'ar samun sauƙi a ko ma menene dake damunta ya yi mata kan ya ajiye babbar ledan da ke hannunshi ya fice, office na Ryan ya koma sai dai ya samu a rufe girgiza kai yayi kan ya juya ya koma nurses station inda ya roki a duba mishi Drn da Ryan yayi referring ɗinta to don ya san ko mutuwa za tayi ba zai sake duba ta ba. Ganin Dr Sulaiman ya sa ya nufi office ɗin nashi. Dukda Captain Saleem zallar soja ne na ƙasa wato land army sai dai tarensu da Ryan ya sa kusan duk wadda ya san Surgeon General Ryan Moh'd Khamis ya san Salim, Salim shi ne ƙwallin abokin Ryan don shi kaɗai ke iya tolerating murɗaɗɗiyar halinshi da zafin Ranshi sam Ryan ba shi da hayaniya kuma ba ya shiri da mai hayaniya, ba ya dogon magana kuma ko da ido yana so idan yayi magana ka fahimce shi bare kuma in ya buɗe baki ya furta ko za ka mutu ba zai maimaita ba, yana da saurin fushi kullum a hasale yake ga ko in kula a koma menene matukar ba shi ya so yin abu ba babu mai mishi dole, sarauta da ƙasaitarshi wane sarki don har wasu kan tambayi ko shi ɗin jinin sarauta ne? A kofan office ɗin yayi knocking aka bashi izinin shiga ya sanya kai, Dr Sulaiman ya miƙe ya bashi hannu suka gaisa kan ya zauna yana dubanshi yace "Dr. Ka san yanayin aikin namu tafiya ce ta kama ni babu zato, zan tafi Kano kuma zan kwana biyu ban san ko za ka iya sallamar ta a yau ba samu in mayar da ita kar in tafi kuma aiki ya riƙeni in kasa dawowa da wuri". Dr Sulaiman ya buɗe file ɗinta ya sake dubawa sossai kan ya ɗago yana kallon Salim ya shiga cewa "A gaskiya cap. Sallama ba zai yiwu yau ba yarinyar jininta yayi ƙasa sossai matuƙa kuma ka san hatsarin hakan, ga damuwa dake dukar zuciyarta shiyasa take ta complain ciwon kai da kirjin dole tana buƙatar kulawar likita atleast na kwana uku zuwa huɗu". Ajiyar zuciya salim ya saki. "Dr Sulaiman ko za ka taimakeni don Allah ka kula da ita har na dawo?" Murmushi Dr Sulaiman yayi "Kar ka samu matsala In shaa Allah zan kula muku da ita, akwai wata tsohuwa dake mana aiki gida zan ɗauko ta ta zauna muku da ita har ku dawo" Godiya sossai salim ya mishi kan ya fice. Ko da ya koma ɗakin ya samu ta farka abinci ya sa ta ci yana ɗan janta da wasa yana mata hira har ta ce mishi ya isheta bayani yayi mata a kan bayan Magrib zai bar garin akwai mai zuwa ta zauna da ita har ya dawo in shaa Allah yana fata kan ya dawo ya samu ta yi sauƙi samu ya mayar da ita gida Fatan hakan ba zai haifar mata da matsala ba? Ta amsa da "uhmm" a ranta take raya a yanzu ko ɓata ta yi ɓat a duniya babu mai neman ta bare ya damu da wanzuwar ta ko akasin hakan, yanzu haka aka tambayeta ina za'a kaita bata sani ba don ko giyar wake ta sha ba za ta tunkari wurin uncle ba dolenta dai shi ne kawu, Nan ma kuma bata san abin da za ta iya riska ba Shikenan ta koma Square Zero? Wasu irin zafafan hawaye ne suka shiga zubo mata. "Afeefah!" 🖤Gureenjoh🖤 HAIHUWA DA HANJI (A True life story) Fatima Muhammad Gurin (Gureenjoh) Wattpad-Gureenjo6763 Arewabooks-Gureenjoh *FREE BOOK* *009* Captain Salim ya ƙira sunan nata cikin tausasawa, ta ɗaga ido ta kalleshi. "Akwai wani matsala ne?" Ta girgiza kai. "Na gode sossai Allah ya saka maka da mafificin alkhairi" Yayi mata murmushi, bai bar ɗakin ba sai ga dattijuwar matar kuɗi masu kauri ya fitar ya ba dattijuwar saboda sayan abinci ya nuna mata kaya kala biyu dogayen riguna da ya siyo da man shafawa, macline, brush, turare da soson wanka ya roƙe ta da ta kula da ita don Allah har ya dawo, kaman kar ya tafi haka ya fice a ɗakin domin haka kawai ya tsinci kanshi cikin tsantsar tausayinta da har yana so ya yiwa zuciyarshi yawa. Baaba jummai macece mai faram-faram da saurin sabo duk yadda Afeefah ta yi shiru sai ta saka ta magana har da murmushi, tana kula da ita sossai sossai, bata maƙe kuɗin da salim ya bata ba ta kan sayo musu kayan daaɗi ta bajo musu tana cewa "Ke 'yannan sa hannu maza ki ga mu ci kin ga ko mutuwa muka yi yanzu za'a ɗauke mu da nishi saboda nauyin mu ina amfanin kana da shi baka ci ba? Maza-maza sa hannu" Dole Afeefah take murmushi kuma ta biye wa Baaba ta ci sossai dare idan an gama duba Afeefar kan su kwanta bacci za ta shiga ba ta labarin aurenta da ma rayuwar da tayi har ma da irin kishin su na da chan baya da kissa kala kala da kan kashe Afeefah da dariya, kan kwana biyu ya zagayo har ta fara manta tarin damuwarta, duk Sallar ta kuwa bata taɓa mance iyayenta da Aunty zee ba ta kan kai wa Allah kukanta musamman cikin dare akan ya gafarta musu yayi musu rahama (Tana roƙon duk wanda ya zo across wannan littafi ya nema musu rahama domin Allah🙏) Kaman yau Dukda safiya ce bayan sun gama karyawa da doya da miya haɗe da shayi da duk a bakin asibitin Baaba ke sayo musu ta dubi Afeefar da ta ɗan yi shiru tana tunani tsoron ta ɗaya dawowar salim ina za tace ya kaita? Ina ta nufa? Ya zata yi? "Wai 'yannan kin kuwa san abin da ke ƙara ba ni mamaki ma a wannan zamanin?" Afeefah ta girgiza kai tana ɗan kakaro murmushi don ta san zancen baaba bai taɓa wuce kan taɓarɓarewar tarbiya a wannan zamani ba. "Mu a lokacin mu ina mace ta isa ta ƙira ko mai irin sunan mijinta? Kai ko bayan ya mutu ko kun rabu mu kam ba ma iya kiran sunan ko da kuwa da kuskure amma ki ji mace yanzu gatsal tana cewa Ummaruuu a gaban yara ma da iyayenshi ko nata kai ko a gyalen su" Dariya Afeefah ke yi sossai tace "Yanzu Baaba ko sakin ki yayi ba za ki iya ƙiran suna mai irin nashi ba?" "Eh mana! Ai da kunya 'yannan" "Tabb baaba ba dai irin sakin wannan zamani ba, komai fa akwai silar chanzuwarshi Baaba bai wuci mazan ma na da na yanzu ba ɗaya ba ne shiyasa ake ganin bambanci" "za dai ki kare su ni dai na faɗa miki ki kiyaye, kin ga maza suna matuƙar son a ba su girma, idan za ki ba namiji girma toh tabbas mutuncin ki ma zai zama daban ne a idanunshi ko da kuwa ya auri wata ne" Tana murmushi sossai tana tuna wato gidan kawu Labaran ban da rashin tarbiya har da tarin jahilci da suke dashi, daga mu'amalar iyayen har ta 'ya'yan gashinan dai gashi nan yo idan ta ciwo shi ai sai dai a ji suna dambe da mata... Fuskanta ɗauke da murmushi tana sake jinjina rayuwar da don baaba jummai na sake bata labarin yadda maƙota sai ya hukunta ɗanka baka sani ba idan ma ka sani ka je har gida ka mishi godiya amma yaran yanzu ko kanwarka ce ka mari yaronta gabanta sai ta maka Allah ya isa a gaban yaro to me yasa ba za'a lalace ba? Haka batun ƙarfafa zumunci Meyasa zumunci ba zai yi ƙarancin ba yara suna 'yan pendo da ɗan kawu amma idan wanchan sun fi kuɗi sai ka ga yana nuna bai san yayyunshi cousins ba ko ya fi karfinsu uwa kuma ta kasa kwaɓa saboda tana ganin hakan ce daidai daga mutum mai kuɗi ne level nashi ya fi karfin talaka ko da kuwa cikin umma ɗaya ne. Turo kofan yayi bakinshi ɗauke da sallama a kanta idanunshi suka soma sauƙa, ajiyar zuciya ne ya kufce mishi ba tare da ya san dalili ba murmushi na yalwatuwa a fuskar tashi ganin ko da suka hada idanu murmushin bai kau daga kan fuskanta ba, fara'a na yi mata kyau ya ayyana hakan a ranshi maganan Baaba ne ya yanke mishi tunani "Bawan Allah sannu da dawowa, lale maraba" Ya saki murmushi ya ɗan rankwafa ya shiga gaisheta ta amsa cike da kulawa tana tambayar shi aikin da sanya mishi albarka, Afeefah ya duba da ta ɗan duƙar da kai tana kallon yatsun hannunta "Na shigo kuna ta raha me yayi miki daaɗi haka Afeefah?" Ta ɗago tana murmushi "Ni da Baaba ne, barka da dawowa" Yana zama gefen gadon tuni ɗakin ya cike da sassanyar kamshin shi ya ce "Yauwa ya jikin? Hope kin samu lafiya?" Ta gyaɗa kai tana dorawa da "Alhamdulillah na gode" Da Baaba suka cigaba da hira akan jikin nata ita dai sai murmushi bata magana har Dr. Sulaiman ya shigo, sai da suka dan sake hira kan ya miƙawa salim takardar sallamar ta "My patient is good to go, kawai dai ta kiyaye sa damuwa a ranta and gaskiya ku kula da ita sossai da sossai Dukda SG Ryan yayi mugun ƙoƙari a kanta babu wani traces na guba a jikinta amma don Allah ku sake kula, ke kuma Afeefah ki saka a ranki komai yayi zafi maganinshi Allah. Manzon Allah S.A.W ya ce; "Wanda ya gangaro daga kan dutse ya kashe kansa, to yana nan madawwami a cikin Wutar Jahannama yana ta gangarawa har abada. Wanda kuma ya sha guba ya kashe kansa, to gubarsa tana nan a hannunsa yana ta kwankwadar ta a cikin Wutar Jahannama, yana madawwami a cikinta har abada. Haka wanda ya kashe kansa da wani karfe, to karfensa na nan a hannunsa yana ta soka wa cikinsa a cikin Wutar Jahannama, yana madawwami a cikin ta hakan har abada. (Sahih Al-Bukhaariy: 5778; Sahih Muslim: 109)". "Allahu akbarr" Baaba jummai ta zabga kabbara Afeefah dai kanta ƙasa zuciyarta na sake shiga cikin tsantsar nadamar wannan yunkuri da tayi da ta mutu ta shiga ukunta. Godiya sossai ta musu haka salim yayi wa Sulaiman da Baba godiya murmushi kawai Sulaiman yayi yana shaida wa Baaba akwai driver waje zai mayar da ita gida sai ga Baaba na hawayen rabuwa da Afeefah Dukda zaman nasu na kwana biyu ne amma sanin ranar sake haɗuwa sai Allah, Afeefar ma sai ta kama hawaye, a duk sadda ta ga wani ya kaunace ta Saboda Allah ta kan ji son shi fiye da yadda shi ya kaunace ta don masu hakan a gareta basu da yawa, bata yi shiru ba ko da Baabar ta tafi sai ma zuciyarta da ya tsinke, tsoro da fargaba suka lallaɓo suka rufe ta. Daram! Haka zuciyarta ya buga a sadda Salim ya ɗauki 'yan kayanta yana furta "Mu je ko Afeefah?" Jiki a saɓule ta sanya kafafunta ƙasa ta shiga takawa har ta wuce shi yana riƙe mata da ƙofa bayan ta fita ya ja kofan a bayanta ya rufe suka jera a tare har motar shi, ya buɗe mata gidan gaba ta shiga ya buɗe baya ya ajiye kayanta kan ya zagaya ya shiga ya ta da motar suka fice daga cikin asibitin, cikin natsuwa yake tukin kan ya ɗan kalleta "Anchau muka nufa ko?" Kamar mai karyayyen wuya haka ta gyaɗa kai gabanta na dukan tara-tara, bata fata Uncle ya raba ta da su suhail bata fata su tashi a hannun kishiyar uwa, daga shi har yaran wani irin tausayinsu take ji har ɓargonta bata ga laifin uncle ba don ta tabbatar dole mutuwar Aunty zee ta jijjiga shi fiye da ƙima tana fata da adu'ar Allah ya sa ya sassauto ya karɓeta kar ya kore ta. Salim ya gyaɗa kai shima, motar ya ɗauki shiru na seconds kan yace "Afeefah!" A hankali ta amsa "Na'am" "Na san kowa abinda yake faɗa miki jarrabawa, kaddara haƙuri. nima ba zan chanza ba don akan hakan Allah ya halicce mu haƙuri kuma da kaddara ibada ne kaman yadda ya halicce mu don mu bauta masa, idan kika ga na wani Afeefah sai kin yi hamdala wani jarabawar shi 'ya'yanshi, wani za ki samu jarabawarshi Mata ne, wani talauci, wani dukiya hatta Mahaifiya ta kan iya zama mummunar jarabawar ɗa, kaman yadda rayyan ya faɗa kuma Sulaiman ya ba ki har hadisi, da kashe kai shine mataki mafi sauƙi a yayin da duniya ta yi wa bawa tsanani da ba za mu tarar da miliyoyin mutane ba a raye, akwai wani hadisi da Manzon Allah S.A.W ya tashi tsoratar da masu yunkurin kashe kansu da ko tunanin aikata hakan ka yi to ka yi gaggawar tuba ka tsarkake zuciyarka daga shaidan. Ban san irin naki ƙalubalen ba amma ina sake jan hankalinki da ki kiyaye dokokin Allah ki duƙufa da Adu'a In shaa Allahu komai yayi farko yana da ƙarshe kinji ƙanwata?" Kai ta gyaɗa mishi a hankali cikin sassanyar Murya tace "Yaya Salim hakika ba ni da bakin gode muku, kun ceceni daga azabar Allah da baku zo ba a lokacin da ban san a yanzu wani hali nake ciki ba. Na gode Na gode Allah ya yaye maka naka matsalolin ya saka maka da gidan Aljanna" Ya amsa da Ameen yana ɗan murmushi. Kaman yadda ta zata isar su Anchau kai tsaye gidan uncle suka yi, ko da ya tura yaro yayi mishi sallama da uncle ba'a jima ba sai gashi ya fito idanunshi na sauƙa kanta yayi mugu- mugun ɗaure fuska bai tsaya ma salim ya gama bashi haƙuri da koro mishi jawabin da ya sa bai dawo da ita kan lokaci ba ranar ya shiga karta musu rashin mutunci yana kwashe mata albarka duk yayi wani irin susucewa, sai jefanta yake da munanan kalamai da suka zama tamkar rurin garwashi a zuciyarta, ya shiga tuna mata Alkhairin Aunty zee a rayuwarta da mugun sakayyarta, ya kuma yi alkawarin muddin bata bar mishi kofan gida ba wallahi shi zai kawo karshenta yayi ajalinta. Kokarin bashi hakuri salim ya shiga yi ganin tana wani irin kuka amma ina tuni ya soma tara musu jama'a babu arziki suka koma mota, ta haɗa kai da gwiwa tana ƙara fashewa da wani kukan mai taɓa zuciyar duk mai saurare. A hankali salim ya ja motar sai da suka yi nisa sossai yayi parking tare da jingina bayan sa da jikin kujerar ya lumshe idanu yana sauraren kukan nata da idan har ka ji ka san duniya bata yiwa mai yinsa daaɗi. Sai da tayi ma'ishi bai ce mata komai ba da kanta ta ɗago ya miƙa mata ruwa ta fita ta wanke fuskanta ta dawo ta sha kaɗan kan ta miƙa mishi ba tare da ta kalleshi ba ya sa hannu ya karɓa. "Ki yi haƙuri Afeefah!" Ta gyaɗa kai "Yanzu ina kuma kike da shi da zan kai ki?" Hawaye ne ya sake cike idanunta a sadda take furta "Akwai kawuna a Dutsen-wai" Cikin dasasshiyar muryarta da ya dishe saboda kuka. Motar ya ja tare da miƙa hannu ya kunna musu ƙira'a domin zuciyarta yayi sanyi. Awanni kaɗan ya sada su da kauyen, ita tayi ta nuna mishi hanya har gidan kawu Labaran. Yana zaune rumfar kofar gida yana cinikin Nono da wata bororuwa ganin tsayuwar mota ya sa ya shiga shafa rantalin kanshi da babu gashi ko guda sai maiƙo yake a rana, a tunanin shi ɗaya daga samarin yaranshi ganɗa-ganɗa da suke zaune ba aure ne domin sun rantse sai mai maiƙo iyayensu mata kuma sun ba su goyon baya alhali gidanshi ko keken hawa mai kafa biyu babu. Idanu ya ƙura mata bayan sauƙowarta yana tunanin inda ya santa kan ya zabura ya runtuma a guje sai cikin gida, ganinshi da gudu ya sa mata da 'ya'yanshi kowa ya fara yin ta kanshi don tsallake su kawai yake bai tsaya ba sai da ya dangana da ɗakinshi ya zaro sandar goran shi tare da wasu manyan layu ya zura a wuya, wasu ya saka a hannu kan ya fito ya nufi waje da saurinshi har yana kifawa.... 🖤Gureenjoh🖤 HAIHUWA DA HANJI (A True life story) Fatima Muhammad Gurin (Gureenjoh) Wattpad-Gureenjo6763 Arewabooks-Gureenjoh *FREE BOOK* *010* "Hohohooo! Da ma an gaya min za ki dawo, za ki dawo da shirin ki da ya ci uwar na da kuma sai ga ki, to idan ma junanki sammako ni a tafe na kwana yarinyaa! Namana guba a bakin ki dodanniyar Mayu!" Yadda yake maganan a kan muryarshi ya sa tuni su inna Asabe suka yo waje, abin ka da ƙaramin ƙauye tuni maƙota ma sun fara leƙowa, daga Salim har Afeefah sun kasa ko da motsi ne barin ma ita da wani tsoro ya sake rufe ta. Tuni matasa suka shiga neman makami don ma kayan sojoji ne jikin salim kuma harda ƙaramar bindigar shi a gefen ƙugunshi. Kawu ya nufa da yake zaro maganganu tamkar sabon kamu wai enchanting words ɗin kariya yake daga Mayu ya furta "Haba Malam! Ba ka gane ta bane? Ya duk ka firgice kaman wanda yayi karo da zaki?" Kawu ya gyaɗa kai ya kuma girgiza yace "Hayyyaa yaro yaro ne! Ni ko na santa farin sani, kai ma na tabbatar da ka san wacece ita babu abin da zai sa ka bari ta shiga motarka. Wannan mayyar da ta cinye min zuri'a ta je ta cinye na uwarta shine ka dawo min da ita kofar gida?" Waigawa salim yayi ya kalleta har lokacin tana kafe kyam kaman mutum-mutumi ya waigo ga kawu hes very confused da kalaman da ake jefa mata gwara wanchan ta ce mijin yapendonta ne amma wannan dake wa ga mahaifinta? Ji abin da yake kaman sabon kamun hauka? "Amma malam ka kuwa san yadda shari'ar maita take? Me yasa za ka jefeta da wannan kalma ta Ƙazafi? Ita ɗin fa 'ya ce a gareka kuma addini kai ya ɗora wa kulawa da ita da bata kariya tunda mahaifinta baya raye amma don Allah dubi abin da kake yi na ƙarancin ilimi, duk ka tara mana mutane? Me yayi zafi haka?" "Wuta! Na ce wuta ne yayi zafi, wallahi idan baka daina haɗa ni da wannan yarinyar ba kai ma sai na rotsa kan ka da wannan sandar bar ganin ka da kayan sojoji, tun muna shaida juna ka ɗauke ta sawunku a likkafa ka mayar da ita inda ka ɗauko ta ai Zainabun ma sai da na gargaɗeta taurin kanta ya ja mata... Ni ma zaman da nayi da ita shekarun baya ban huta ba da neman kariya da yanzu babu wanda za ka tarar anan da duk ta lashe kurwowinmu" Ya hayayyaƙo wa salim da baƙin ciki haɗe da wani irin takaicin su ke shirin kashewa, ita dai ban da kuka babu abin da take kaman ranta zai fita hannayenta duk biyu bisa kanta jikinta na wani irin rawa. Ya godewa Allah da ba da Rayyan ya zo ba yau da kuwa yanzu wani zancen ake ba wannan ba, duk haƙurin salim sai da su kawu suka kai shi bango, ya kaɗa ya rawa a kan su karɓeta sai dai cin mutunci kawai suka karta musu da kalamai masu zafi suka ma fara yunkurin far musu da sunan haushin ta dama suke ji haka ya dauƙeta suka wuce suka bar garin gudun fitinar da zai iya kunno kai idan suka ci gaba da tsayuwa. Shiru ne ya ratsa motar sama da awa guda sai tsula uban gudu yake ita kuma tana ta aikin kuka. "Afeefah ya isa haka don girman Allah ki yi haƙuri, ki karɓi wannan ma a jarabawa. Akwai inda zan kai ki kuma?" Yayi maganan yana kallonta, ɗago ido tayi ta kalleshi sai da ya ji wani yarrr a jikinshi ganin yadda idanunta suka koma tsabar kuka, ɗauke kai yayi har ƙasan Ranshi yana jin ɗacin da bai sani ba baƙin cikin su kawu ne ko menene oho. "Ba Za ka tambayi wacece ni ba? Ba ka ji kana son sanin ni ɗin Mayyar ce da gaske ko akasin hakan ba? Ba ka ji kana tsoro da shakkar taimakona ba?" Ta faɗa cikin dasasshiyar muryarta har lokacin idanunta na a kanshi. Ya samu wuri yayi parking kan ya waigo gabaɗaya yana kallonta "Ki gane wani abu Afeefah, Na riga na saka a raina taimakon ki ya zama min dole. Batun sanin ko ke wacece ba zan ce miki bana son ji ba amma ba na son tilasta ki ba ni labarinki, idan muna tare watarana zan sani. Ba na tsoron ki don ke ɗin ba Abar tsoron ba ce ba kuma na Fatan yin da na sanin taimakon ki" Yana kallon cikin idanunta ya ƙarasa maganar, zuciyarta ne ya sake karyewa hawayen da suka tsagaita sai suka fara shirin dawowa sabo, kaman da wasa ta shiga sanar mishi da tarihin rayuwarta daki-daki tun daga farko har kawo ranar da ta sha guba don ta kashe kanta. Numfashi ta ja sam bata duba yanayin shi ba ta cigaba da cewa "Na gode kwarai da taimakon ka da kuma yarda da ni da kayi ba tare da ka san ni din wacece ba, ba na so in sake ɗora maka wani nauyi ko damuwa ba kuma na son wani abu ya same ka ta dalilina. Za ka iya ajiye ni anan kawai ka bar ni ka koma gida Na gode sossai..." Idanunshi da suka sauya sossai suka cika da tarin kwallar tsananin tausayinta da rauni ya ɗauke bisa kanta yana lumshe su da ƙarfi, ya rasa ma kalar tunanin da zai yi wani irin tausayinta ke bin gaɓoɓin jikinshi yana kassara su, ji yake kaman ya taya ta kukan ta ɗauki abubuwa dayawa fiye da shekarunta, tabbas dole tayi yunkurin kashe kanta don duniyar bata dandana mata daaɗi ba sai akasin hakan, hakika ya yabawa hakurin ta da tarin juriyarta da wani ne ko guba bai kashe shi ba damuwa sai yayi bindiga da zuciyarshi. Sama da mintuna uku ta sauƙe numfashi ta sa hannu ta buɗe kofan tana shirin sauƙa ta ji ya kira sunanta "Afeefah!" Waigowa tayi tana kallonshi, ya rankwafa ya janyo murfin da ta buɗe ya rufe kirib kan ya kalleta "Ba zan iya barin ki anan ba Afeefah! In na ce ma ki sauƙa anan za ki yarda?" Ta Yi shiru ya sauƙe numfashi kan ya ta da motar yana mayar da idanunshi bisa titi ya shiga ja a hankali. "Sunana Salim Mahmud ni haifaffen nan jahar ne na Kaduna, ni ne ɗa na farko a wurin iyayena kuma namiji tilo ina da ƙanne mata uku Sadiqa ke bi na Dukda akwai tazarar shekaru masu dama tsakanin mu sai Sameerah kan Auta Samha dukkansu suna jami'a ne presently. Tun Samha na da shekaru uku a duniya muka rasa mahaifin mu ya saura daga mu sai mommy, dangin mahaifin mu suka watsar da al'amurranmu duk da kasancewar mahaifina mai karamin ƙarfi bai tara mai yawa ba, kuma duk yawan da zai tara akwai hidimomi gabanmu ya sa tun ba a je ko ina ba komai ya ƙare, mahaifiyar mu ta matukar shan wahala da mu kuma ta yi ɗawainiya mai yawa da ba don tayi karatu ba ma da bamu san halin da muke ciki ba a yanzu, bata huta ba sai da ta ga ta kafa ni ta yadda zan iya taimakon ƙanne na. Mahaifiyar mu macece mai tausayi sai dai duniya kuma ta koya mata son nata don bata haɗa soyayyar yaranta da kowa ba. Ban sani ba ko za ki iya zama cikinmu idan kin amince zan je na roƙe ta, zan bata labarinki za ta ji tauaayinki kuma in shaa Allah za ta haɗa ki da su Samha ta rungume mu cigaba da rayuwa har Allah ya kawo miki miji ki yi aure". Kuka take mishi mai sanyi, ashe har tana da zaɓi a yadda taken nan? Har sai ta ce ta amince zata zauna da su ko da naman jikinta za su dinga yankewa da tayi bulayi a titi? Kalaman godiya tayi ta jera mishi yana hana ta don gabaɗaya rauni da tausayinta sun sassara mishi gaɓoɓi da yake jin zai iya joining ɗinta su yi kuka tare. Yamma sossai suka dawo cikin Kaduna, daga ita har shi babu mai magana idanunta zube a titi, masu hidimar komawa gida kawai take kallo Dukda zuciyarta ya jima cikin nashi duniyar, kwakwalwanta ya zurfafa a tunanin wani irin ƙaddara ne kuma ya dawo da ita cikin Kaduna? Shin za su amshe ta bayan sun ji labarinta ko za su kore ta? Idan suka kore ta ina ta nufa? Akwai mai sake mutuwa sanadiyar ta? Anya ta yi mishi adalci da ta biyo shi? Har suka isa cikin Unguwar rimi bata sani ba, jin ƙarar horn na mota ya sa ta ɗan yi firgigit ta dawo da hankalinta kan inda suke sai ta tsince su a wani layi mai jerin rukunin gidaje iri ɗaya. Gidaje ne masu kala ɗaya kusan komai na gidajen Layin iri ɗaya ne bambancin kawai lambobin da ke maƙale gefen kyauren ko wani gida, Baƙin gate ɗin aka zuge wani matashi ya shiga yiwa salim ɗin barka da dawowa hakora a washe, Salim ya tsaya suka gaisa kan ya nausa cikin tsararren madaidaicin gidan da ya tafi da imaninta, harabar shimfide da interlocks an ƙawata gidan da shukoki jajaye, shudi, kore da ma wasu kalolin ma su ban sha'awa. Ginin da kaman an zana ne ba a gine yake ba saboda yadda yayi mata kyau gidan sama ne, harabar gidan shiru babu kowa har ya shigar da motar cikin ma'ajiyarta tsakanin wasu motoci madaidaita guda biyu. Hamdala yayi yana zare keyn ya dube ta "Mu je ko?" Babu musu ta gyaɗa kai ta buɗe kofan ta sauƙa, shi ya buɗe bayan da ya fito ya zaro ledar da 'yan kayanta ke ciki suka nufi cikin gidan yana gaba tana biye da shi a sanyaye, a gaban mashigar gidan suka dakata ya danna doorbell, babu jimawa aka buɗe Brown security door ɗin wata kyakyawar yarinya da za ta iya girme mata ta gani tsaye, haɗa idanu da suka yi da Salim ya sa ta saki ƙarar murna kan ta sauƙo da gudunta ta faɗa mishi tana dariya sossai shima yana murmushi ya tarbeta ya ɗan yi hugging ɗinta kaɗan ya sake ta "Welcome home bro" "thanks Autar Hajiya mommy" Ta saki murmushi tare da jan hannunshi suka yi ciki tana ihun sanar da isowarshi, hakan ya sa wasu 'yan mata biyu suka fito su ma a guje suna mishi maraba, yanayin kamanninsu ya sa ta tabbatar da su ne ƙannenshi da ya bata labari, murmushi take saki don sun matuƙar burgeta har tana jin ina ma da ba ita kaɗai aka haifa ba, ita kam ba ta da wannan gatan Allah bai ba ta ba bata gama tunanin ta da murmushi ba ta ga Fitowar wata dattijuwar mace da suke matukar kama, fuskarta cike da fara'a har hakwaranta biyu na hajji na bayyanuwa, doguwa ce kaman su salim da suke dogaye, haka ba ta da wani ƙiba don idan ba a yanayin fuska da ya bayyana girma ba ba za ka ce ta haife su ba. Ganinta ya sa salim ya ture ƙannenshi ya isa yayi hugging nata "Oyoyo Mommyna" "Welcome home my son, idonka kenan?" Ya sake ta yana ɗan shafa kai, ta saki murmushi ta san ya kan shigo cikin Kaduna amma sungulollinshi ba ko yaushe yake bari ya ƙaraso gida ba, kusan satin shi uku zuwa huɗu rabon shi da su sai a waya. "Wannan kuma wacece yaya? A ina ka samo ta?" Samha da tun bayan gama murnar su ta ƙure Afeefar kur da idanu tayi tambayar. "Samha Afeefah sunanta, ki kaita ɗakin ki ta yi sallah ki ba ta abinci idan na sauƙo bayan isha za mu yi magana" Babu wanda ya sake tankawa a cikin su har ya haye sama inda nan ne sashen shi, ta duƙa ta shiga gaishe su ɗaya bayan ɗaya sai ƙare mata kallo suke suka amsa ba yabo ba fallasa. "Mu je" Samha ta furta mata, ledan ta da samhar salim ya ajiyewa ta ɗauka mata ta nuna mata, babu musu ta sa hannu ta ɗauka ta bi bayanta. Bayi ta nuna mata ta shige a lokacin har an fara kiraye kirayen Sallar Magrib, Allah ma ya sa ta zauna da Aunty zee da take da 'yan abubuwan zamani Dukda bai kai na gidan ba amma ta iya ta buɗe tayi alwala ta fito. Samhar na zaune bakin gado tana latsa waya ganin Fitowar ta ya sa ta nuna mata gabas ba tare da ta bata sallaya ko ta motsa daga inda take zaune ba, sai da Afeefar ta shimfide dankwalinta a saman tiles ɗin kan Samha ta miƙe ta shige bayin. Afeefah na sallah ta ji samhar na wanke bayin ko da ta idar samhar ta fito ta shimfida sallaya daga chan nesa ta tada Sallar ta, ko motsi Afeefah bata yi ba tana ta Adu'a da roƙon Allah a kan wannan rayuwa da za ta yi a wannan gida, har aka kira isha kan ta miƙe ta gabatar Adu'a ta cigaba da yi a kan kar Allah ya kawo ajalin wani tana cikin gidan, tun bayan Magrib Samha ta fice daga ɗakin bata wani jima da idar da Sallar ba tana zaune kawai sai ga samhar ta turo kofa ta shigo. Plate na shinkafa jollof ne ta ajiye mata da wani karami mai dauke da ruwan leda guda biyu. "Na gode" Ta faɗa, kai kawai ta gyaɗa ba tare da ta buɗi baki ta amsa ba ta sake ficewa. A chan parlor kuwa bayan salim ya shigo daga Sallar isha suka ajiye mishi nashi tray ɗin dake ɗauke da plate na shinkafar da wani an yi wrapping salad da wani saucer mai ɗauke da pepper chicken da ke fidda kamshi haɗe da zobo jug guda. Bismillah yayi ya shiga ci a natse don ya tara yunwa sossai a cikin nashi, sai da ya gama yayi hamdala hajiyar su da tuntuni idanunta ke kanshi ta ce "Salim yarinyar chan da ka shigo da ita daga ina haka? Meyasa take a waje har bayan Magrib ba za'a nemeta a gida ba?" Ya ɗan gyara zaman shi "Wallahi Mommy yarinyar ce rayuwarta abin tausayi, na rasa me yasa mutanen mu suke haka a wannan rayuwa ashe don ajalin bawa yayi ya amsa ƙira sai ya zama lallai lallai wani ɗan uwansa mutum ne ya kashe shi? Duk mun manta cewa idan ajali ya zo babu mai jinkirta wa ko da da second guda ne sai ya tafi?" Hajiyar ta gyara zama tana katse mishi hanzari "Hakane idan har mutum ya mutu ajalin shi ne ya riga yayi amma a komai akwai sanadi" Ya ɗan yi jimmm yana kallonta for seconds kan ya shiga magana "Mommy Afeefah Marainiya ce! Mahaifinta ya rasu tun tana ciki, mahaifiyarta ta rasu wurin haihuwar ta...." A hankali ya cigaba da ba su labarin Afeefah kaman zai zub da ƙwallah har kawo yanzu, yana sauke aya Samha ta miƙe hannunta duk biyu dafe da ƙirji idanu waje ta ce "Mayya Yaya Salim???" 🖤Gureenjoh🖤 https://chat.whatsapp.com/Ef0BFnE69VjAhuWCV9Fxbe?mode=ems_copy_t HAIHUWA DA HANJI (A True life story) Fatima Muhammad Gurin (Gureenjoh) Wattpad-Gureenjo6763 Arewabooks-Gureenjoh *FREE BOOK* *Kun ga comments? To ku dage da comments za ku sha mamaki amma idan bakwa yi haka nima zan ke shantakewa. A takaice dai ina roƙon ku da ku ba ni haɗin kai mu ga mun gama labarin nan cikin watan nan don kowa ya sanni ya san ba na Littafi mai tsawo* *011* Wani irin kallo ya watsawa Samha da ya sa ta koma ta zauna sai kuma ta fara hawaye, juyawa yayi ya kalli hajiyarsu da tunanin za ta yi mata faɗa sai ya ga ma kallon shi take da expression na mamaki a fuskanta. "Mayya fa ka ce Salim? Shi ne za ka tura ta ɗakin autana ta fara da ita? Me ya hau kanka da za ka kawo mana cutarwa gida after all faɗi tashi da muka sha don mu ga mun inganta rayuwar mu?" Kasake yayi yana cigaba da kallon mahaifiyar tashi bai taɓa tunanin zai fuskanci wani matsala daga Mommy ba, ya zaci ta san zafin ɗa kuma ɗan wani ma zai iya zama nata musamman idan ta ji cewa Marainiya ce don ta fi kowa danɗanar wahalar da maraici ke janyowa. "Mommy na ɗauka Afeefah Abar tausayi ce da muddin na ba ki labarinta za ki karɓeta hannu bibbiyu, ki rungumeta tamkar su Samha wallahi mu ma Allah zai dube mu ya ba mu ladar kula da ita" "Dakata Saleem! Dakata min don Allah! Ka kawo yarinya kana ikirarin danginta sun guje ta saboda Mayya ce da tun tana ciki take cin maita ta ci har uwar da ta haife ta da ubanta ka kuma yi expecting in karɓeta? Ta cinye min ku kenan? Ko ni kake so ta cinye maka? To ba da ni ba salim... Ba a gidan nan ba maza maza tun dare bai ba tarkatata ka mayar da ita inda ka ɗauko ta tun muna shaida juna je ka fitar min da yarinyar nan a gida ba za mu taɓa shiryawa ba..." Hankali tashe ya ɗan kalli kofar ɗakin Samha kar Afeefahn ta ji ya matso ya riƙe hannun mommyn. "Mommy wallahi ba gaskiya ba ne duk fa zargi ne da Ƙazafi irin na mutanen duniya, wallahi Afeefah is innocent mommy ki tausayawa rayuwarta don Allah. Mu ma fa marayu ne ki saka ta a sawun su Samha idan da ɗaya daga cikinmu ne ake yiwa wannan kazafi za ki iya jura? Za k...." A hasale ta katse shi "Na rantse da Allah zan tsinka maka mari salim ka sake alaƙanta yarana da wanchan Abar, eh ku marayu ne amma da ba ku ci naman kowa ba uban wa yayi muku Ƙazafi? Bari ka ji ba'a taɓa yaɗa jita-jitar da bashi da kamshin gaskiya ba. Kafin na hasala na haɗa da kai ka je ka fitar min da yarinyar nan a gida..." Samha da har lokacin take hawaye tace "Innalillahi wainna ilaihi rajiun ni dai mommy wallahi ba zan iya sake shiga ɗaki na ba" Sadiqa tace "Ni dama daga ganinta na ji har ga Allah bata kwanta min ba, sai nuƙu-nuƙu take ashe babu gaskiya a lamarin ta" Sameera ta yi kwafa "Nan ma ba ki ga idanunta bane, duk abin tso..." "Kun yi min shiru ko sai na sassaɓa muku? Da ku nake magana ne? Ko na kira sunan dayanku anan? Kun ga kun yi kama da waenda zan nemi izininku kafin aiwatar da abin da yake daidai? Duk cikinku akwai wacce ta isa ta hanata zama a gidan nan ne?" Ya daka musu tsawa Ranshi ya kai ƙololuwar ɓaci duk mommy ce ta ba su wannan ƙofa amma ya zai yi? Gaban mommyn ya koma ya kama hannunta idanunshi kaman garwashi don saura kiris ya fara yi mata kuka a yadda yake jin zuciyarshi ya ce "Don girman Allah mommy kar ki koreta, ba zan iya bari ta tafi ba mommy in ta fita a gidan nan ina za ta je? Musulma ce fa 'yar uwarmu kuma mace, ko don aikina na kare lafiyar al'umma mommy ba zan iya tura Afeefah waje ba, Don Allah mommy ba don ni ba ki sake nazari akan hukuncin ki kar ki saka ni yin abin da zai yi hunting ɗina for life please mommy" Ganin zai kai gwiwar shi ƙasa yana cigaba da roƙon ta ya sa ta riƙe hannunshi suka koma zaune, wuri guda ta tsurawa idanu sama da mintuna biyu ta sake kallonshi duk ya marairaice yana roƙonta, Salim a yaranta yana da haƙuri yana kuma da kawaici don da wuya ya roƙe ta abu ko ya tambayeta ko da kuwa yana matuƙar bukata ko da kuwa buƙatar kuɗi ne, yana tausayinta ƙwarai gani yake har yanzu bata huta da ɗawainiya ba alhali, gidan gadon su ma 'yan haya ne ciki bai san ya suke kashe kudin ba a haka shi yake daukar ɗawainiyar karatun ƙannenshi da cin su, tufafin su da ma sauran hidima na rashin lafiya bai taɓa gazawa ba tun da ya riƙe ƙasa to Meyasa za ta kasa yi mishi wannan alfarma guda? Amma kuma idan yarinyar ta kashe mata shi fa? Numfashi mai matuƙar nauyi ta sauƙe ta ji ana cewa Mayu sun fi cinye kurwan wanda ya taimaka musu ya ji tausayinsu kenan muddin yarinyar za ta zauna gidan sai ta cire wa salim tausayinta? Amma ta yaya? Ta sake jan ajiyar zuciya cikin gamsuwa da shawarar zuciyarta "Shikenan Salim na amince ta zauna amma fa ina da sharuɗɗa, sharrudan da zan gindaya maka wanda matuƙar ka tsallake Allah ya isa ban yafe maka ba" A firgice yake kallonta, zuciyarshi kaman zai fito waje jikinshi har yana wani rawa don ba ya wasa da Abin da ya shafe ta, me yayi zafi da Allah ya isa? Da kyar ya iya buɗe bakinshi da yayi masa nauyi ya furta "Allah ya isa mommy? Ni??" Ta gyaɗa kai cikin alamun tabbatarwa tana kawar da idanunta daga kallonshi kar ma ya bata tausayi kuma ta san muddin ya amince ba zai taɓa tsallakewa umarnin ta ba. "Sharuɗɗan su ne babu ruwanka da abin da ya shafe ta, za ta zauna zan bata abinci sau uku kaman kowa, za ta yi aikin da ya kamata a ce kowacce mace na yi saidai duk wani abu da ka ga na yanke a kanta babu ruwanka, do not question me a kan duk abin da ya shafe ta i repeat! Magana ta fatar baki tsakanin ku in har ya wuce minti ɗaya ban yafe maka ba, ni zan duba in ga cancantar saka ta makaranta ko akasin hakan idan zaman ba na ɗore bane dole za ta bar gidannan ka kuma yanke kowace alaqa tsakanin ku, ko da ko sannu ne" Ya yi jimmm kanshi ƙasa duk ya damu kan ya sauƙe numfashi "Shikenan mommy in shaa Allahu zan kiyaye umarnin ki" Yana kai nan ya miƙe ya bar musu parlorn Ranshi na ƙuna, da yana da mata babu abin da zai hana shi riƙe Afeefah tamkar 'yar sarki ya ba ta ingantacciyar rayuwa, a yanzu ma bai fidda tsammani ba ya amincewa mommy ne da tunanin with time za ta sassauto daga kudurinta. Tuni suka cika parlorn da hayaniya bayan barin shi suna uzzurawa mommyn akan me yasa ta amince da zaman yarinyar gidan? "ku yi shiru ku bar ni da shi, ai in bata ga wurin zama ba da kanta za ta fitar da kanta daga gidan ba sai wani ya kore ta ba." Ta miƙe ta nufi ɗakin Samha tana jin abin da zuciyarta ke gayamata daidai ne, duk suka rufa mata baya wane sarauniya da fadawarta. Suka sameta zaune inda take tun bayan idar da Sallar ta idanunta suna zube a farantin abincin da ko loma uku bata yi ba saboda tunani da ya ci karfin kwakwalwanta, tsoro ne sossai da fargaba suka danne yunwar da take ji don rabonta da abinci tun da suka karya da Baaba da safen a asibiti. "Ya ma Sunanki?" Mommyn ta tambaya tana sake ƙare mata kallo. "Afeefah" ta amsa a hankali. "Ban san wani kalar tsafin kika yi wa Saleem ba da har karo na farko ya zaɓi bijirewa umarni na a kanki, amma bari mu ga ko ke kin san hallaci? Zan ja miki federal warning akan yarana don ni karan kaina ban san abin da zan iya aikatawa ba a kansu, hawainiyarki ta kiyayi ramata idan kina cin ƙasa to fa ki kiyayi na shuri wallahi ko da wasa 'ya'ya na suka yi ko da ciwon kai ne hmmmm" Ta kara hmm ɗin da wani irin siga na razanarwa, "ana magana ba za ki amsa ba?" Sadiqa tayi maganan tana hankada ta da kafar ta A ɗan razane ta gyaɗa kai. "Tashi in kai ki inda za ki zauna, ki ɗauki farantin nan don daga yau a ciki za'a na baki abinci har Allah ya raba mu da ke, kuma ba ki isa a saka miki abinci ki bar mana ba don a nan ba ma almubazzaranci da gumi muke nema don haka dole duk abin da aka saka miki haka za ki cinye. Shara, mopping da wanke-wanke su ne aikinki. Am I clear?" Sameera tace "Kai mommy ke ma ina wannan ina jin turanci? aka ce kin fahimta?" "Eh na fahimta" Ta amsa cikin rawar murya. "Tashi mana ni ki bar min ɗaki, ko za mu tsaya muna jiran ki ne?" Dole ta miƙe da sauri ta ɗauki kayanta da plates ɗin ta bi bayansu, ta kofan baya suka fita suka miƙa har Boys quaters jin hayaniya da hira haɗe da dariya kuma Muryar maza ya sa ta sake tsorata, isan su varender ɗin Hajiya ta shiga buga cikin aihinin main building ɗin ɗaya daga cikin su ne ya leƙo ganinta ya sa ya koma da gudu ya ƙira sauran suka fito su uku. Ba manya bane chan matasa ne duka masu jini a jika da fafutukar neman halal, Ishaq shi ne ke musu wanki da guga sai iliya da shi ne driver sai mudi mai gadi, ganin duk maza ya sake tsorata Afeefah me hajiyar take nufi? A sama ta ji muryarta tana cewa "ke! Ga ɗakin ki nan" Tq nuna mata wani single room dake kan varender ɗin. Da gaske a waennan garadan za ta haɗa ta, ganin yadda suke kallonta kaman kura ya ga nama ya sa hawaye ɓalle mata a take tana ji hajiyar na cewa "Mudi wannan itace mai wanke-wanke da share share za ta zauna a ɗakin nan kar in ji kar in gani" "To! To hajjaju in shaa Allah za mu kiyaye" Suka juya suka tafi suka barta nan tsaye kyam. "Sannu kyakyawa" Bata tanka ba sai shige wa ɗakin da aka kira da nata da tayi da gudu ta datse kofan tare da zamewa a jikin kofan tana fashewa da kuka sossai. Dariya suka sheke da shi don tayi mugun basu dariya suna shiga ɗaki kuma suka fara gulman kyaunta, kaman daga sama suka ga an turo kofa da ƙarfin gaske duk razana suka yi sai kuma a take suka wani irin zubewa ƙasan ganin Saleem riƙe da bindiga muraran, fuskan nan yayi Red babu wanda zai iya cewa ya taɓa ganinshi cikin wannan yanayin a take jikinsu ya tsume cikinsu ya shiga ba da ƙarar tsoro suna tunanin me suka yi? Iliya ke ta maimaita "Yau mun shiga uku mun lalace allurar ce wallahi ta tashi a kanmu ya Allah ga mu gareka.." Kuuuuu haka kowa cikinshi ke ba da sauti ganin ya sake haɗe fuskan nan tamau, ya samu hannun kujera ya zauna tare da ɗora kafan shi daya kan kujerar ya sa bindigar ya ɗan sosa goshinshi yadda za su sake gani da kyau su tabbatar, ya sauƙar yayi kooking ta ba da sauti tuni suka maƙale juna suna kakkarwa kaman kadangarun da suka faɗa wuta sai salati suke. Ya ce cikin dakakkiyar murya "Menene wannan a hannu na?" Mudi da yake jin yana shiru saleem zai iya fashe kanshi don an sha ce musu idan allurar sojojin ta tashi bata da hankali ana ɓata wa sojan rai sai kisa yayi carab ya ce murya na rawa "Abin kashe mutane" "sunanta na tambaya!!" Ya faɗa a hasale da kuma gaske a mugun hasalen yake, Ishaq yayi saurin cewa "Sunanta bindiga wallahi bindiga sunanta" "Kun dai san ni soja ne, kuma ina da lasisin harbata ko?" Sai kai suke gyaɗawa kaman kadangaru "Buɗe baki za kuyi ku amsa ni malamai" Tuni suka cika ɗakin da "Eh, tabbas! Haƙiƙa hakane!" "To ku buɗe kunnuwanku da kyau ku ji ni, wannan yarinya da Hajiya ta kawo ta nan ko kallon da ya wuce na seconds kuka yi mata bare magana ta fatar baki ba tare da kwakwaran dalili baaaa..." Ya miƙe tsaye ya isa inda suke ya ɗodɗora bindigar kan kowannen su yace da ƙarfi "Toh tabbas sai ya kwana a lahira!!! Ina Fatan kuna ji na da kyau??" Suna zare numfarfashin tsoro da kaɗuwa suke amsawa a tare "Mun gane wallahi mun gane, ba za mu kuskure ba ranka ya dade yallabai" Ya ɗan matsa baya. "Kar ku ga kaman ban cika zama ba, gidannan ko ta wani ɓangare ina da abin ɗaukar video a ɓoye waninku ya gwada saɓa doka ta ya gani..." Yana kai nan ya juya ya fice bayan ya sake nunnuna musu bindigar a Goshi ai da gudu iliya da mudi suka fara rige-rigen isa bayi sai zawo...! Ko magana cikinsu babu wanda ya sake yi a haka baccin dole ya kwashe su dukunkukune da juna. Ya ɗan jima tsaye yana kallon kofan ɗakin nata bayan fitanshi kan ya wuce, yana tsaye a balcony ɗin shi na sama ya ga isar mommy da ita wurin abin ya matuƙar damun shi, ta ya mommy za ta haɗa mace da maza har uku waenda ba muharammanta ba? Tsoro ne ya mamaye zuciyarshi ba zama yake ba yana matukar tsoron wani abu ya sameta ba zai iya yafewa kanshi ba, wayanshi ya fitar ya kira Rayyan. Ringing na ƙarshe ya ɗaga da sallama "Ya aka yi ne man?" "I need your advice, ni ne na kawo lu'u lu'u mai tsananin daraja da ƙima sai na rasa inda zan killace hakan ya sa dole na ajiye a inda ba ni da tabbacin za ta samu tsaro da kular da ta dace da darajar ta, ban gama nazari ba sai na kyalla ido na hango wasu kananun ɓarayi da basu kai ko da shakar numfashi ɗaya ba suna zagaye wannan lu'u lu'u da kallon da ban gamsu ba, idan ba zan iya tafiya da wannan lu'u lu'u ba kuma dole zan tafi wani mataki kake ga ya kamata in ɗauka?" Ryan ya ɗan yi shiru na seconds kan ya ce cikin dakakkiyar voice ɗin shi "Dukkan yanki ba'a rasa ɓarayi kuma ko wani ɓarawo yana da uban gida, idan har kai ne uban gidan wannan ɓarayi kana da dama da ikon gargaɗi mai zafi irin na asalin maza ba mata ba, ina mai tabbatar maka daga zarar sun tsorata da gargadin ka ko kallon hanyar da wannan tagulla take ba za su sake ba" Lumshe ido yayi "Na gode" Ryan ya kashe wayanshi. Ya ɗan sake nazari kan ya saki murmushi ya juya ya je ya ɗauko bindigar ya wuce sashen. Dariya kaɗan yayi tuna yadda suke ta zazzaro idanu suka jike jagwaf da gumin tsoro... 🖤Gureenjoh🖤 HAIHUWA DA HANJI (A True life story) Fatima Muhammad Gurin (Gureenjoh) Wattpad-Gureenjo6763 Arewabooks-Gureenjoh *FREE BOOK* *Don Allah ku yi haƙuri da wannan yau ɗin nan ban zauna ba wallahi* *012* Ta ɓangaren Afeefah anan bakin ƙofa ta ci kukanta har bacci ya sure ta ba tare da ta sani ba, mummunar mafarki da tayi da Aunty zee ne ya sakata farkawa a razane, fitsari ne kaman zai zube mata hakan ya sa tayi single kofa guda ɗaya da ta gani a ɗakin sai ta samu madaidaicin bayi ne, bayan ta gama abinda take ta fito ne ta fara bin ɗakin da kallon tsanaki don wutar a kunne tarrr kaman rana. Matsakaicin ɗaki ne a lailaye yake da farin tiles, fanka da bulbs duk suna aiki daga chan dungu 'yar ƙaramar katifa ce da babu ko shimfidi a kai, sai agogon bango da ɗakin ke dashi, time ta kalla ƙarfe biyu na dare har ma da mintuna ashirin da uku, juyawa tayi ta koma bayin ta yo alwala ta zo ta sake shimfida dankwalinta ta saka hijabinta ta tada sallah, raka'a shidda tayi a sujadar ƙarshe ne ta saki kukan dake dukanta a kirji tana jerowa Allah kirari bayan ta jera sunayen shi masu daraja casa'in da tara ta bi da salati annabi kan ta fara jero matsalolin ta da neman sassauci ta yiwa iyayenta da sauran 'yan uwanta da ta rasa Adu'a ta roki Allah ya kawo mata sauƙin rayuwa ya warware mata matsalolin ta ya kuma cigaba da bata zuciyar karbar ƙaddarar ta a duk yadda ya zo mata. Kusan ƙarfe uku da rabi ta sake kwanciya a wurin sanyin tiles na ratsa ta har wani baccin ya ɗauke ta. Ta makara don tana bude idanunta ta ga haske daga Window, da sauri ta miƙe ta shige bayi tayi saurin yin alwala ta zo ta gabatar da Sallar asuba tana sallame wa bata wani zauna Adu'a ba don tsoron laifi abincin jiya da ya ƙanƙare saboda sanyi ta cuccusa kan ta fito riƙe da plate ɗin ta nufi inda ta ga sun fito jiya. Tsaye bakin kofan kitchen ta ci karo da mommy sanye da hijabi, duk da zuciyarta ya buga haka ta ƙarasa ta zube a ƙasa tana gaisheta. "Sannu isasshiya sai yanzu za ki fito? Ban gaya miki aikin ki shara da wanke wanke bane, sai karfe nawa ake shara a gidan ku?" Murya a sanyaye tace "Ki yi haƙuri" Tsaki ta ja kan ta juya cikin kitchen ɗin "Talatuwa miƙo mata kayan sharar nan da mopping ta ajiye su chan baya don bana son kallonta gangar abincin da yarana za su ci ban san me za ta iya jefawa ciki ba ko jini ko tsoka" Abubuwan sharan wata dattijuwar ta fito mata da su, ta karɓa ta fara share parlorn zuwa dining area daga nan bayan ta gama ta shiga mopping da goge-goge aiki ba baƙonta bane don wannan a wurinta mai sauki ne sossai ma, haka zagi ko hantara duk ta riga da ta saba sai dai ba rayuwar da take fata tayi ba kenan, ba rayuwar da take buri ba kenan tana so ta ga tana karatu tana so ta ga tana hulda da mutane kaman kowani dan Adam, tana so taga ana hira da dariya da ita kaman yadda ta samu gidan Aunty zee, sai dai da kaman wuya wai guguwa da auren nesa. A gefe ta tsaya tana kallon Talatuwa dake ta aikin shirya abincin mutanen gidan bisa dining bayan ta gama ta dubi Afeefah tace mata "Ki zuba turarukan wuta 'yan dai-dai a cikin wanchan abin ki kunna" ta ƙarasa tana nuna mata burner, show glass ɗin ta tafi a hankali cikin natsuwa ta buɗe ta ɗauko ta saka ta kunna yadda aka gaya mata ta koma bakin kitchen ɗin ta tsaya tana cewa Talatuwa ta gama.. "Akwai abincin ki na saka miki a plate ɗinki ki ɗauka kije ki ci sai yaran sun gama karyawa tass sun wuce makaranta ake wanke-wanke" Da to ta amsa kan ta ɗauka ta fice, a hanya ta gamu da Ishaq so take ta gaishe shi amma kaman walƙiya haka ya wuce ta, bata damu ba ta shige ɗakin da yake da sunan nata ta rufo kofan. Ba za ta ce rayuwa a gidan yayi mata tsanani ba, saboda kwata kwata aikinta bashi da yawan da zai dameta, tana idar da Sallar asuba take zuwa tayi share share da su goge goge ta ɗauko abincinta daga nan ta tafi, sai wuraren sha ɗaya take komawa dining ta tattaro duk abubuwan da suka ɓata na karyawan ta fitar waje ta wanke ta kawo bakin kitchen ta ƙira talatuwa ta shigar, lokacin ita kuma Talatu za ta fiddo mata da abubuwan da ta bata na rana za taje ta tara su wurin wanke wanken ta rufe ta ɗauki abincin ranar ta ta tafi, sai bayan la'asar za ta fito tayi wanke-wanken haka na dare sai wuraren takwas tara. Ba Ta da abokin hira don talatuwa tsakaninsu ki yi kaza ne kar ki yi kaza ita kuma amsar ta ɗaya a komai to. Su iliya gudunta suke bata sani ba ko sun samu labarin ita ɗin annoba ce oho, bayan Hajiya da suka gamu sau ɗaya 'yan mata ukun ko ganinsu bata sake yi ba, kaman yadda bata sake saka saleem a idanunta ba tun ranar da ya kawo ta zuwa yau da take neman sati uku. Bata sani ba shin rayuwar zai cigaba da tafiya a haka ne ko zai sauya? Shikenan ta sallamar da burin ta na yin karatu kenan?Shikenan ta tabbata Mayyar za ta ci gaba da rayuwa ita kaɗai tamkar a fursuna kenan? Bata da mai bata amsa. Da misalin ƙarfe biyu na dare chan cikin baccinta ta ji kaman ana buga mata ƙofa, a ɗan tsorace ta farka sai ta ji ana ambaton sunanta "Afeefah! Afeefah!!" Tun ranar da ta sanya kafafunta cikin gidan yau ne karo na farko da ta ji sunanta na fita a bakin wani hakan ya sake razana ta, da ta kasa kunne kuma sai ta ji kaman Muryar salim a maimakon ta ji sauƙi sai ta ji tsoro ya sake dabaibaye ta. Me yake yi a kofar ɗakin ta da wannan tsohon daren? Ashe bai ma manta da ita ba yadda tayi tunani? Miƙewa tayi ta nufi kofan wani zuciyar na cewa idan kuma hajiyarshi ta ganshi fa? Allah ya isa fa zata mishi sanadiyarta, sai ta girgiza kai tana dakatawa. "Afeefah saƙo zan baki ki buɗe don Allah, na san kina jina please buɗe ba zan jima ba" A hankali yayi maganan amma ta ji shi tsaff kasancewar dare ne, ta gyaɗa kai tana ba zuciyarta tabbacin saƙo kawai zai bata ya juya ba wani abu bane, da sauri ta je ta buɗe kofan sai suka tsaya chakk idanunshi cikin nata yana ƙare mata kallo kusan seconds biyar bai ce komai ba sai ita ce tayi ƙarfin halin ɗauke idanunta daga kanshi ta ɗan duka ta ce "Ina kwana Ya salim?" Ɗauke idanunshi yayi ya lumshe su kaɗan ya saki ajiyar zuciya mai dan nauyi, matsota yayi sossai ta matsa baya tana kallonshi da manyan idanunta, ya leƙa ɗakin kaɗan kan ya dawo baya, time ya kalla inda seconds ke reading, babbar leda jumbo dake hannunshi ya ajiye mata don baya so ya shiga ɗakin nata ba da wannan dare ba, kai ko da rana ne ma baya jin zai iya kebewa da ita inuwa guda ko don addini da ya haramta hakan. "Ki kula sossai za mu yi magana" Yana kai nan ya juya ya fice, ta bishi da kallo har ya ɓace mata kan ta runtse idanunta tana kokarin mayar da kwallarta ta tura kofar ta rufe, ledan da ya fi ƙarfinta ta shiga ja har gaban katifa ta barshi nan ba tare da ta buɗe ba tayi kwanciyar ta, sai dai duk yadda ta so baccin ya sake ɗaukar ta baccin ya ƙi zuwa, tuni ta buɗe idanunta ledar ta janyo gabanta ta shiga buɗewa a hankali. Da wani bargo mai taushi ta fara cin karo kaman ya san tana matuƙar bukatar bargon don tana shan wahalar sanyi da aka fara shiga, gashi bayin ta babu ruwan zafi wani lokacin hatta alwala da kyar take iya yi, wanka kam ba'a magana in dai tana so tayi sai ta bar ruwan a rana wuraren sha biyu zuwa karfe biyu nan ma da kyar za ta watsa bata gama tunanin ba ta ci karo da kwalin heater, irin wanda ake maƙalawa jikin bokiti ɗin nan a kunna ta ɗora shi kan bargon tana ɗan murmushi, ta sake mayar da hannunta ciki ta zaro hijabai ninkakku har kala huɗu kuma duk za su iya kai mata ƙasa Brown, Ash, purple da onion colour su ma gefe ta ajiye su, ta sake mayar da hannu ciki ta zaro kananun catons na biscuit da wasu small chops dai waenda za su dan kwana biyu basu lalace ba daban daban masu ɗan yawa, har da su five Alive kananu catons uku. Ganin abubuwan dake ciki sun kare ta ɗaga ledan domin matsarwa don ta sake kallon sayyayarta sai taji da ɗan motsi a ciki, ta buɗe gabaɗaya ta ci karo da ƙaramin kwali jikinshi da zanen waya, buɗewa ta yi ta ci karo da karamar Villion mai kyau da tsari Dukda keypad ne amma sossai ya mata kyau, fuskar wayan ne yayi haske alamun a silent yake saƙon akwati na SMS ya bayyana tare da sunan. "Saleemullah" Sai ta saki murmushi karo na farko ta buɗe saƙon. "Ba ki yi bacci ba?" Numfashi ta sauƙe kan ta shiga reply don ta iya sossai a wayan Aunty zee da ma wasu 'yan ajin su na islamiyya lokacin da take zuwa makaranta ta amsa da "Eh, Na gode sossai da saƙon ka duk abinda ka saka a ciki kaman ka san ina da buƙatar su" Bata ajiye wayan ba ta ƙurawa screen ɗin ido chan sai ga reply ɗin shi. "Na kasa samun natsuwa da tunaninki zuciyata ita ta lissafo min duk abin da zuciyarki ta raya tana da buƙata. Kin ga ko zuciya bata ƙarya" Ta karanta saƙon ya fi sau abin da ya fi sai ta rasa amsar bashi, bata motsa ba har wani saƙon ya sake shigowa daga gareshi. "Na san baki jin daaɗin yadda kike zaune amma kiyi haƙuri zan yi iya ƙoƙarina in ga na yi settling komai, za ki yi karatu har sai kin ce ya isa, ga wayan nan zan dinga yi miki saƙo ki tabbatar kina yi min reply, duk kuma abin da kike so do not hesitate ki sanar da ni zan kawo miki. Akwai full qur'an a memory ɗin idan kin ji kaɗaici ki rage lokaci da shi kin ji?" Tana murmushi a lokaci ɗaya idanunta na zubar da kwalla ta rubuta "Wallahi samun mai irin zuciyarka sai an tona Yayana, na gode na gode Allah ubangiji ya ba ni ikon saka maka" Ta tura tana murmushi "Never mention my dear, ki kwanta kar ki makara da safe byeee" Ta sake sakin murmushi kan tayi reply "Allah ya ba mu alkhairi Soja Mai kirki" Dariya yayi daga ɓangaren shi ya rubuta "Au akwai marasa kirki ne?" "Eh mana, abokin kan nan Dukda gaskiya ya faɗa amma in a wrong way, su ne suke ɓata muku suna ake yi muku kuɗin goro" Ya girgiza kai yana cigaba da murmushi "Ryan kenan! Haka Allah yayi shi, oya sleep Good night" Bata yi reply ba sai lumshe idanu da tayi razanannun idanunshi da yake zare mata su da sautin dakakkiyar muryarshi suka dawo mata kaman yanzu yake yi, da sauri ta buɗe idanun gabanta na faɗuwa ganin ita kaɗai ce sai ta saki murmushi a hankali ta maimaita sunan "RYAN" tana lumshe ido. 🖤Gureenjoh🖤 HAIHUWA DA HANJI (A True life story) Fatima Muhammad Gurin (Gureenjoh) Wattpad-Gureenjo6763 Arewabooks-Gureenjoh *FREE BOOK* *013* Sabo ne mai ƙarfi ya shiga tsakanin su ba na wasa ba ta sanadiyar wannan text message da suke yi wa juna, yana matuƙar wuya ta sanya shi a idanu amma baya yini ya kwana ba tare da sun ɗauki mintuna masu ɗan dama suna exchanging SMS ba, sai dai idan inda yake babu network, idan kuma tana aiki ne wayan na maƙale a kunnenta tana sauraron karatun alarammar Prof Isa Ali phantami wato sheikh Abba zari'a yana matuƙar yi mata daaɗi har ta roki Saleem da in zai zo ma ya taho mata da alqur'ani ta cigaba da koyo don yadda yake karatun daidai da 'yan koyo. Yau ya kama Lahadi kusan duk iyalan gidan suna a gida in ka cire salim da rabon shi da gidan ma an kwana biyu, da zazzabi ta tashi tana jin sanyin hunturu dake busawa na Huda jikinta, kasancewar koyaushe hannunta na ruwa ne ko tana bakin pampo kuma sossai bazarar ya shiga hakan ya haifar mata da mura da ta ɗan kwana biyu dashi, a maimakon ya ragu ma na safiyar yau worst ga ciwon kai mai tsanani da take fama da shi ko idanunta bata iya buɗewa da kyau, a hankali kuma karo na ba adadi ta ɗago su da kyar ta kalli agogo kusan ƙarfe tara na safe ko shara bata yi ba gashi babu wanda ya leƙo ta bare a yi mata uzuri, lallaɓa wa tayi ta miƙe tsaye atishawa na ƙwace mata da ƙarfi ta ja hanci tana dafe kai haka ta sauƙa ta zari hijabai har biyu ta sanya saboda yadda a ɗaki ma sanyin ya isheta bare ta fita waje, a hankali take tafiya har ta isa main parlorn gidan daidai kofar kitchen ta hadu da Talatuwa. "A'a yanzu kenan zan tafi biɗar ki, na gama abin kari tuntuni ina son fitarwa kuma ba'a yi shara ba. Lafiya kam?" Ta ja hanci tana ɗan dafe kanta dake juyawa "Wallahi mura ne ke damu na sossai, kaina kaman an ɗora min dutse" "Ashhaa! Sannu Allah ya baki lafiya, idan Hajiya ta fito ki gaya mata za ta baki magani. Yanzu ki je ki kwanta bari ni na yi sha...." "Ta Yi mene? Kwanciya ta zo yi gidan ne da masu gida suna kwance itama tana kwance?" Sadiqa ta katse musu zancen da gadara. "Wai na ga bata jin daa..." "Kinga Talatuwa ba dake nake ba, ki je ma ki fara shirin ɗorawa friends ɗina abinci za su shigo babu jimawa, ki tabbatar abin da za ki dafa zai ishi cin mutane shidda zuwa bakwai... Ke kuma" Ta juya ga Afeefah "Ki wuce ki je kiyi aikin ki, kuma ki tabbatar tana gamawa ba'a ajiye mana kwanuka a mawanki kudaje suyi ta bi ba" Kai Afeefah ta gyaɗa bata ce komai ba ta wuce ta ɗauko kayan sharar ta duƙa don fara wa, da ƙarfi ta runtse ido jin kanta kaman zai biyo ta ya faɗo haka ta cigaba da aikin cikin dauriya irin nata, Sadiqa dake tsaye tana danna waya rashin maganan yarinyar ke matukar bata haushi ta ja doguwar tsaki kan ta juya fuuu tayi ɗakinta. Afeefah ta gama sharan tana mopping kenan ta ji zuban kaya bisa saman kanta, baya baya tayi Allah ya taimaketa ta dafe jikin dining table, ta ɗago rinannun idanunta ta zubawa Samha da ta watso mata kayan... "Ni ki daina kallona, kurwata kurrr... Wa ma ya sani ko naman wanda ya fi ƙarfin ki kika ci ya tsaya miki a wuya. Ki gama abin da kike ki wanke min kayannan sameera ta aiki Ishaq kuma ina da bukatarsu babu jimawa". Bata jira amsar Afeefah ba ta wuce zuwa ɗakin Sadiqa, dukkansu biyu suna zaune ne Samha ta isa tace. "Allah da gaskiyar ki Aunty sadiqa yarinyar nan ta samu wuri har wani iyayi take kaman ta Allah, muka cigaba da zuba mata ido babu wanda ya san me gaba za ta haifar kin ga har wani fresh tayi ta kara kyau" Sameera tace "Ni na fi tausayin Yaya Salim don daga ganin yarinyar nan wallahi green snake ce, bana tunanin idan da Mommy bata ɗauki matakin da ta ɗauka kanshi ba zai rayu har yau, gwara mu kasheta da aiki ta yadda zata gaji ta gudu" Sadiqa tace "Toh ai yanzu sai mu ci ɗamarar hakan don na ga mommy ta fara mance zancenta, kin ga idanunta kuwa? Wlh muddin yarinyar nan ta samu rana ba karamin shanya za ta yi ba". Suka cigaba da tattaunawa akan Afeefah da idan an matse su ba za su iya faɗan laifinta guda a gare su ba amma da yake amfani da zancen mutane ya riga ya zama jinin ɗan Adam sai ya zamana kawai da gaske Mayya ce a gare su kuma idan bata bar gidan ba za ta iya raba ɗayan su da rayuwarshi, haka kuma duk wanda ya nuna mata tausayi to fa shi za ta fara lamushewa. Zaune yake cikin mota da alama abu yake dubawa don hankalinshi duka ya tattaru ne ga wayan hannunshi, sanye yake da wani grey trouser mai taushi ya haɗa ta da cream Color shirt da yafi yanayi da gashin mage tsabar taushinsa, high neck ce wuyan don idan da zai ja daga sama zai iya rufe har hancinshi da rigar, Dukda wani irin sanyi da hazo da ya cike sararin samaniya motar dake kunne cike take da sassanyar iskar Ac ya haɗu da ni'imtacciyar kamshin shi da ma flavours da yake amfani da su na motan suka ba da wani kamshi na musamman. A hankali sautin waƙan Alex Warren ta ordinary ke tashi, tsaki ya ja a karo na barkatai a ranshi yake shirin fara masifa don baya ƙaunar bata lokaci sai ga wayanshi ya shiga ƙira, Bluetooth na kunnenshi ya ɗan danna. "Allah Saleem zan yi tafiyata ka san na tsani ɓata lokaci" Duk da a hankali yayi maganan alamun muryarshi ya nuna ya hasala kuma tabbas zai iya tafiya ɗin don saleem ya shiga masa lokacinsa. "Afuwan mutumina wallahi sai yanzu na tuna inda papers ɗin nan suke, suna ɗakina kuma kyakyawar ɓoyo na musu babu wanda zai san inda suke ban zaci boss zai tambaya bane da na taho da su, please help me ka je ka dubo min" Shiru yayi saleem ya marairaice murya "Please help a soul ba ni da mai min sai kai, ka ji Autan Mammi?" Da magiya ya ƙarasa hakan ya sa Rayyan ɗan murmushi "Don dai kai ne..." "Eh taimaka pls" Ko kan salim ya gama maganan ma ya ja motar cikin natsuwa yana sauraran kwatancen da saleem ɗin ke mishi na inda safe ɗin da ya ɓoye confidential files ɗin yake, Saleem ya bashi wahala don ya fi hour yana neman su a office nashi na nan head quater don mance inda ya ajiye yayi sai daga baya ya tuna da kyar. Daga waje Ryan ya ajiye motar shi ya sauka ya shiga cikin gidan da ƙafa cikin tafiyar shi mai cike da ɗumbin ƙasaita wane saraki hannayenshi duk zube a aljihu, waƙa still yake ji a Earpods ɗin kunnen nashi saidai sautin na fita ne da sanyi ba mai hayaniya ba, kamar ko yaushe a murtuke fuskar nan sai kace wanda aka zagi iyayenshi har ya shige, bai nufi ma main parlorn ba ta kofar baya ya zagaya ya haura stairs da zai sada shi da ɗakin salim, a jikin kofan ya tsaya ya duba inda suke ajiye key ya ɗauka ya buɗe ya sanya kanshi ciki don duk sun san inda ɗayansu ke barin spare key incase of emergency, dulum ɗakin don komai a kashe ya kunna wuta ya wuce uwar daka direct wardrobe da ya mishi kwatance ya je ya buɗe, kaya ne a jikin hangers ɗin ya ware bangon ya bayyana gefe wani keypad ne da ba zaka ce akwai wani abu da zai iya buɗuwa ba ko da an danna. Wasu numbobi ya saka sai ga wardrobe ɗin ya dare, ya turo wani box waje nan ma ya saka wasu lambobin sai ya budu bai tsaya ma duba me ke ciki ba ya zaro files ɗin ya buɗe don tabbatar da shi ne ko ba shi ba, su ɗin ne kuwa yana ƙoƙarin scanning dilim nepa suka ɗauke. Ɗakin ne yayi duhu sossai ba zai iya scanning haka ba sai ya nufi balcony door yana dan tsaki ya buɗe ya tsaya daga saman ya fara scanning yana forwarding to salim dake online yana jira har ya gama, yana ƙoƙarin mayar da wayan aljihu ya ɗan ɗago sai idanunshi suka faɗa kan ta, har ya juya ya ɗan dakata ya sake waigo wa ya kalli ƙasan ba fuskarta yake kallo ba irin aikin da take yi a sanyin yake gani a ranshi yana raya 'Mutane are heartless' Ya dai san babu ɗiya mace mai gata da zata zauna a wannan uban sanyin tana wanki ga tarin wanke-wanke dake jira a gefe, bai ga dacewar a ce kowa na ɗaki a ɓoye ita ɗin tana ƙasan pampo ba, bai gama tunanin ba ta saki atishawa har huɗu a jere ta ja hanci tare da ɗora goshinta a kan gwiwarta, wani iri yaji sai yaji yana son kallon fuskarta, hakan ne ya hana shi tafiya har ta ci seconds kan ta ɗago ya ɗan ƙurawa face ɗin idanu. Kawar da idanun yayi ya mayar hannunta dake wani irin rawar ɗari duk kakkarwa suke, sun sandare saboda sanyi ga hijaban da ta lafta rabi a jiƙe shakaf. Tunanin inda ya san fuskan yake sai dai ya kasa ya ɗan sake kallon gashin idanunta da suka yi fari fat ya ja tsaki tare da barin wurin gabaɗaya, mayar da takardun yayi ya fice daga sashen ya nufi harabar gidan don tafiya sabgar gabanshi sai ga Sadiqa ta fito taryar Ƙawayenta da Shigowar su kenan kowacce na ƙoƙarin sauƙa a motar ta, ganin shi ya sa ta wani zaro idanu shi kam kallo ɗaya tak yayiwa gefen da suke ya ɗauke kanshi ya cigaba da tafiyarshi with steez bai ma san su waye ba bare ya tantance mutane ne ko aljanu. "Ya Ryan" Ta ƙira sunan a hankali sanin baya son ihu ko hayaniya, in ka cika ko magana da ƙarfi ne sai Ranshi ya ɓaci kuma muddin nashi ya ɓaci kaima sai naka ya ɓaci haka yake, ya ɗan ɗago ya kalleta a kan rigar sanyi jibgege dake jikinta ya soma sauƙe ido kan ya ɗan ja tsaki matsalar shi kenan, da wuya ya ga abin da ke cutar da wani ya iya ɗauke kai, baya son zalunci sam a rayuwarshi Dukda ana yi mishi kallon miskilin mai murɗaɗɗiyar hali sai dai yana da tsananin tausayi, 'yan aikin gidansu sun shaidi hakan don shi mutum ne dake so ya ga an baiwa ɗan Adam haƙƙinsa na mutum cikakke kaman yadda Allah ma ya karrama dan Adam ya kuma ba shi daraja. Yanzu dubeta killace cikin shigar da ba zai bar iskar bazarar cutar da ita ba amma 'yar aiki zaune ƙasan pampo hannayenta da kafafunta duk cikin ruwa cikin halin rashin lafiya don a matsayinshi na likita kallo daya tak yayi mata ya san bata da cikakken lafiya hakan sai ya sake ɓata Ranshi amma sam fuskanshi na nan a yadda take bata sauya ba "Ina kwana? Ashe ka shigo?" Kai ya gyaɗa kawai ya zagaye ta ya wuce abin shi, da kallo ta bishi tana murmushi a fili ta furta "Miskili ka fi mahaukaci ban haushi" "Waye shi?" Ɗaya daga cikin Ƙawayenta da duk suka bi shi da ido yuuu tayi tambayar. "Ryan Khamis kike ji da gani, sojan da ko a cikin sojoji ake ji dashi, likitan da ko a cikin likitoci babu kamarsa... Ga sanyi ga zafi, ganin dariyar shi ko murmushinshi sai ka yanki tikiti" "Wow shi ne Surgeon General Ryan Khamis? Da gaske don Allah? Dama yana zuwa gidanku haka a bati?" Sadiqa ta saki murmushi "Abokin yayana ne, yana zuwa sossai ma musamman idan suka samu saukin aiki saleem na gida don ba'a raba su, mahaifiyarshi ma na zuwa har gidan nan, shine dai Ryan Khamis" No 1 matashi ne da ake ji dashi mata suke rububinshi don duk inda ya shiga akwai masu kyasawa amma fa shi duk basa gabanshi, yana flatforms sai dai babu wanda ya san handle nashi don akwai handles dayawa da sunayenshi na ƙarya ana yaudarar 'yan mata, shi dai kam kaman dutse yake mace bayan mahaifiyarshi duk a maza Ƴan uwanshi ya ɗauke su. Da zancen shi suka shiga parlor nan aka baje ana cigaba da hiranshi kala kala da kyar suka saki suka kama wata. Shi kam Rayyan yana tada motar shi ya danna ƙiran Salim "Don iskanci ko godiya ba za ka min ba ko?" "Afuwan Ryan ka san ina gani printing kawai nayi na tafi presenting don ana jirana, yanzu kenan fitowa ta ko wayan ban fitar ba na ji ƙiran ka" Driving yake slowly duk zantukan Salim ɗin bai tanka ba sai ya daka tsalle ya kama wani zancen da ya kasa bari a ranshi sai yake jin kaman shima Allah zai kamashi da laifin wulakanta dan Adam tunda ya gani bai yi magana ba "I saw someone familiar kaman na san fuskan but i cant recall" Salim ya ɗan tafi nazari kan ya ce "A gidan mu kuma?" Kai Ryan ya gyaɗa sai kuma ya tuna voice call ne suke yi a hankali yace "Yeah, choculate tall young lady haka" "Afeefah ka gani?" Salim yayi saurin katse shi, a ranshi ya maimaita sunan 'Afeefah' ba tare da yayi magana ba, Salim ya cigaba da magana "Ka santa mana Rayyan, yarinyar da ka ceta wacce ta taɓa shan poison a Anchau?" Sai lokacin ya tuna inda ya san fuskar but Meyasa take aikatau gidan su salim? Ina iyayenta da family ɗinta? Kaman salim ya shiga Ranshi wai aka ce sanin hali ya fi sanin kama bai wuce magana ne a bakinshi ya kasa fitarwa ba don haka ya shiga bashi labarin yadda ya mayar da ita da irin wulakancin da suka sha yadda ta bashi labarinta daga farko har karshe sai da ya gama tsaf Ryan dake parking tsakar gidansu ya ce "Hmmm" Ya ƙarasa yana dan taɓe jajazir ɗin laɓɓanshi ba tare da ya ce komai ba bayan nan, har salim ya zaci ya katse kiran sai ya ji Ryan ɗin ya watsa mishi tambayar "Then taimakonta kenan ka yi to be lowly house help?" "No! No!! Wallahi ba hakan bane a raina Rayyan na rasa yadda zan yi ne, mommy ta katange min duk wata ƙofa da zan iya inganta rayuwarta, abin is hurting me badly... Ka kuwa san akwai Allah ya isa a kaina muddin na yi magana da ita na fatar baki na sama da minti ɗaya?" Ɗan zare shanyayyun idanunshi Rayyan yayi "Wow! Why?" "Saboda kawai sun yarda da champin mutane da ƙagen da ake yi mata" nan ya shiga bashi labarin gumurzun da suka sha da mommy a kanta kan ma aka barta a house help ɗin. Rayyan ya ɗan lumshe idanu ya buɗe a ranshi mamakin mutane yake yi, Sai ji salim yayi yana cewa "Idan bata kashe ku ba ku ai kun ɗauki hanyar kasheta!" Yana kai nan ya yanke wayar don ya gaji da magana, ɓalle murfin motar yayi ya nufi cikin gidan cikin natsuwa da takunshi na ƙasaita haɗe da izza. Kasake salim yayi rike da wayan a hannu yana juyawa, jikinshi ne ke bashi ba haka kawai Rayyan yayi maganar Afeefah ba, ya kuma san a yanzu ko ya sake kiranshi ba lallai ya bi ta kan zancen Afeefah ba kuma bare yayi mishi bayanin me yake nufi da za su kasheta? Hankalinshi ne ya ji yana neman tashi. Allah ya sani daga lokacin da tausayinta ya yi tsanani a ranshi ya juye ya zama mishi so ba tare da ya farga ba, har ranshi sonta yake kuma so yake ya aureta saboda ƙaunar da yake mata not out of pity, ko da ya ajiye ta kaman yadda mommy ta umurta yayi iya kokarinshi wurin ganin ya manta da rayuwarta ya bar wa mommy ɗin sai dai hakan ya gagara mishi dole ta sa ya waiwayeta ya dawo ya kawo mata waya don ya dinga jin lafiyarta da bukatun ta, layinta ya lalubo ya zubawa idanu sama da mintuna uku kan ya danna mata ƙira sai da ya jera sama da 10missed calls bata ɗaga ba sai hankalinshi ya fi na da tashi ya tura mata text message sama da biyar ba reply. A lokacin tana ƙoƙarin tattara kwanukan da ta gama wankewa ta kai bakin kitchen, jikinta babu inda ba ya rawa har hakwaranta na haɗuwa, bayan ta ajiye ta koma inda ta tashi ta ɗauki wayan da karatun ma yau bata samu ta iya kunnawa ba ta nufi ɗakin tana tafiya da kyar, hijaban kawai ta zare ta zubar a wurin ta shige bargo tana hawayen tausayin kanta, jin kaman vibration na wayan nata ya sa ko ido bata buɗe ba tayi picking tare da maƙalawa a kunnenta, Sheshekarta ne ya fara shiga mishi kunne yaji wani abu ya sauka mishi har cikin zuciyarshi hakan ya rikita masa lissafin kwakwalwa... "Afeefah menene? Me ya sameki?" Shiru sai kuka da itama jin muryarshi ya sa ta ƙara karfin kukan, kaman shi ma zai fashe da kukan cikin sanyi ya shiga cewa "Don Allah ki yi min magana Afeefah, hankalina tashi yake da kukan nan naki talk to me please, menene?" Sauƙe wayan yayi ya kalli time saura seconds goma "Help me Afeefah ko ta text ne ki rubuta min Meke damun ki? Kar ki yi kisan kai ki taimaka" Yana kai nan ya sauƙe wayan ya kashe tare da jingina kanshi jikin motarshi, ji yake kaman yayi tsuntsuwa ya ganshi Kaduna sautin Muryar kukanta ke ta amsa kuwwa cikin kanshi... 🖤Gureenjoh🖤 HAIHUWA DA HANJI (A True life story) Fatima Muhammad Gurin (Gureenjoh) Wattpad-Gureenjo6763 Arewabooks-Gureenjoh *FREE BOOK* *014* Shigowar saƙo wayanshi ne ya sa da wani irin hanzari ya miƙe daga jikin motar yana duba wa. "Ba ni da lafiya" Abin da kawai ta iya rubutawa kenan, sai ya ji hankalinshi ya fi na baya tashi don bai san wa zai kira ya taimaka mata ba, idan ma ya ƙira su Samha ya san abin ba zai yi kyau ba mommy kuma za ta iya ɗaga hankali a kan ya aka yi ya san bata da lafiya yana Maiduguri tana Kaduna? Wani tunani ne ya faɗo mishi, nan ya shiga neman Layin wani friend dinshi da yake nan capital hospital Kaduna ɗin a kan ya taimake shi da Layin Dr. Sulaiman, cikin mintuna biyu sai ga Layin a take ya shiga ƙiran Layin ringing uku aka ɗaga "Dr Cap. Saleem ne don Allah wani taimako ne nake nema daga gareka please in ba damuwa" Ya faɗa bayan sallama da gaisuwa, Nan ya yi ta mishi godiya bayan sun gama disussing, ko gida bai iya ya je ba yana zaune ne kawai cikin motar shi cike da tsumayin sake ganin ƙiran Sulaiman. A chan Kaduna kuwa sallamar da ake ta doka wa ne ya sa sameera Miƙewa ta nufi ƙofan, Sadiqa suna dining da Ƙawayenta ana cin abinci ana hira, mommy ke karyawa a tsakiyar parlorn, Samha na wani research a system ɗinta hakan shine ma ya tilastawa sameera da ke danna waya Miƙewa tana mitar irin uban Sallamar da ake tayi, tana bude kofan ta yi niyyar masifa ne sai idanunta suka sauƙa kan Dr. Sulaiman da ke jingine ɗan nesa kaɗan da jikin motar shi, daga ganinshi ka san responsible matashi ne da yake kan ganiyar samartakarsa daga yanayi shiga da kuma tsarin motar shi zaka san ko shi ba mai kuɗi bane daga gidan kuɗin ya fito, Baaba jummai ce dake doka Sallamar ta katse ta "Har na fara tunanin babu mutane ne gidan 'yan nan ashe kuna ciki" Ta ɗan harareta a fakaice "eh muna nan, lafiya kam?" Ta ƙarasa tana sake kallon Dr. Sulaiman da har yanzu hankalinshi ke kan wayanshi. "Wanchan likitan Afeefah ne mun zo duba ta da jiki" Ta haɗe fuska kan tace "Ina zuwa" Ciki ta koma kafin mommy ta tambayi waye ta shiga ce mata "Mommy wai sun zo duba wanchan Mayyar da yaya salim ya kawo wai likitan ta" Ɗan shiru mommy tayi tana tunanin Allah ya sa ba salim bane ya aiko su, sai kuma ta tuna ai bai ma san halin da take ciki ba, kila ma ya zuwa yanzu ya mance da ita ko ma bai mance da ita ba ta san ba zai taɓa saɓawa umarnin ta ba itama kuma hankalinta ya fi kwanciya a yadda yayi uwar watsi da rayuwar yarinyar yake kuma mu'amala da ita da ƙannenshi lafiya ƙalau. "Tura Talatuwa ta kai su, su suka sani" Ta ɗan zauna kaɗan kan ta miƙe ta nufi ɗakin Talatuwa ta tura ta, Baaba jummai har ta gaji da tsayuwa sai ga Talatuwa, suka gaisa kan tace su tafi ɗakin Afeefar don yadda ta gantan nan ta tabbatar ba za ta iya fitowa ba, Dr. Sulaiman Baaba ta yiwa magana ya bi bayansu har ɗakin da Afeefar take su biyu ya bari suka fara shiga, Baaba jummai na ta sallalamin yadda ta gantan kan ta fito ta kira Sulaiman cikin sauri "Alhaji ƙarami zo ka ga yarinyar nan jiki babu daaɗi sam" Ita kaman uwa take wurinsu don gabanta aka haife shi har ya girma tana gidan su, kuma shine babba a yadda ya ɗauke ta kaman uwa haka ƙannenshi suka tashi suka gani su ma kuma suka yi following footsteps ɗin shi a girmama ta, shiga dakin yayi ya isa gabanta ya duƙa. "Afeefah" Ta amsa da "uhmm" ba tare da ta buɗe idanunta ba. "Menene yake miki ciwo?" Ta Nuna mishi kanta da kaman zai tsage. "Akwai amai?" Ta girgiza kai. "Jiri fa?" Ta gyaɗa kai. "Mura fa da tari?" Nan ma ta gyaɗa kai, plate na abincinta na safen da ke rufe a gefe ya buɗe ko spoon ɗaya bata yi ba. Ledojin da ya shigo dasu a hannunshi ya shiga buɗewa babu bukatar zuwa asibiti drip ya haɗa ya ɗaura mata ya haɗa allurai yayi wasu a jikin canular wasu kuma jikin ruwan, ya dubi Talatuwa "Kin san magungunan da suka shafi na mura da zazzabi da sa bacci, bare ma jininta ya yi ƙasa sossai tana ɗan buƙatar hutu na kwana biyu ba tare da ta yi hulda da ruwa ko abu mai sanyi ba" "Toh fa, ranka ya daɗe ni ma 'yar aiki ce kamar ta ba ni da ikon bata hutu da dai Hajiya da kanta ka yi wa bayanin da sai ya fi" Ita dai Baaba jummai ta zabga tagumi tana kallon Afeefah dake bacci ji take kaman ta yi mata kuka ashe itama aikatau take yi gidan su Saleem ɗin? Muryar Sulaiman ne ya katse ta yana cewa Talatuwa "ko za ki kai ni wurin hajiyar?" Duk da basu yi haka da Saleem ba amma ba zai iya kau da ido a kan yarinyar ba she's too young and fragile kaman she's having a lot a cikin zuciyarta. Fitowa suka yi Baaba dai kaman ta tsaya haka take ji Don Allah ya saka mata ƙauna da tausayin Afeefah kaman jikar ta. Talatuwa ta duƙa gaban mommy bayan ta bar su a waje "Hajiya da ma wai likitan ne yake son gani ki". Kan mommy ta yi magana ma sameera tayi saurin cewa "Ki ce ya shigo, mommy bari na ba ki mayafi" Samha ta ɗago ta kalleta, mommyn bata ce komai ba har sameerah ta kawo mata mayafin daidai Sulaiman ya yi sallama ya shigo. Kamshinshi ne ya cika parlorn duk yadda mommy ta so ta kame nagartarshi da kwarjininshi ya sa ta shiga mishi sannu da zuwa a dole, gaisheta ya shiga yi cikin girmamawa bayan sun gama Sameerah ta shiga gaishe shi, ya amsa da murmushi saman fuskanshi dole Samha itama ta gaishe shi itama ya amsa mata kan ya dubi mommy "Da ma akan patient ɗi ta Afeefah na nemi ganin ki Hajiya, na zo duba jikinta don ganin lokacin komawarta checkup ya yi ban ganta ba sai na samu ashe tana kwance rip da zazzabi mura da kuma low BP da ya addabe ta" Mommyn ta yi kaman bata san bata da lafiya ba tace "Asshaa ka ga aikin rashin wayaun Afeefar ko? Babu fa wanda ta sanar wa bata da lafiya, mutum kullum a maƙale a ɗaki ya ba za'a yi zazzabi ya dame shi ba? Allah dai ya kyauta" Sulaiman ya ɗan murmusa don wannan ba hujja bace a gareshi idan kai ka kula da mutum ba lafiya ba sai ka jira ya gaya maka ba, haka kuma idan baka ji mutum ba ana dai zaune tare kai ke da alhakin leƙa wa ka ji shin yana lafiya? "Ai duk alamun rashin lafiyar ne Hajiya, a likitance duk wadda ba ya son interracting da kowa ya fi gane kaɗaici da rashin magana yana shiga ƙuncin ko damuwa duk akwai alamar tambaya kanshi, Don Allah a taya mu kula da ita idan tana samun kulawa in No time za ta ji sauƙi ta komawa aikinta in Shaa Allah" Sameera ta riga mommy magana "In shaa Allahu Dr. Za mu yi duk yadda ka ce Allah ya bata lafiya" Yayi mata murmushi kan ya amsa da Ameen itama dai fuskar nan cike da fara'a take ta kallonshi. Mommy ta ce "Ba na son ka faɗawa Salim, ka ga yana wurin aiki kar ya zaci ba ma saka ido ne a kanta duk hankalinshi ya tashi, bills ɗin ka dinga turomin zan ke covering" Ya gyaɗa kai kawai yana kokarin Miƙewa Sameera tace "Ko ruwa baka tsaya ka sha ba?" Ya ce "No na gode, ai daga gida na fito" Daga an suka fice suka bar su. Wayanshi ya zare bayan ya yiwa motar tashi key ya ɗan zubawa Layin salim ido yana nazarin abin da ke faruwa, Salim ya ce kar mamanshi ta san shi ya turo su, mamansu ta ce kar salim ya san Afeefah bata da lafiya to me kenan? Ɗan shrugging Kafada yayi kan ya danna ƙiran salim yana ficewa daga harabar gidan, kaman jira ko ringing na farko bai yi ba salim ya ɗaga "Ya ya jikin nata Dr.? Is it worst? Sai an tafi hoapital ko?" "Calm down Captain jikin da sauƙi" Nan ya shiga koro mishi bayanin yadda suka yi da mommyn. Numfashi ya sauƙe bai wani ji damuwarshi ya ragu ba don ya san da matuƙar wuya su bi ta kanta, roƙon Sulaiman yayi da akan ya dinga zuwa yana duba masa ita kaman yadda yayi alkawari. Yana dan murmushi yace "ba ka da matsala in shaa Allahu" "Thank you so very much Doctor" "Ɗo not mention" Daga nan suka ajiye wayar. "Oh ashe wannan baiwar Allahn aiki take gidan su salim ɗin?" Baaba tayi maganan da alama dai har yanzu tana jimamin yadda suka tafi suka bar Afeefah ɗin. "Ni ma sai yau nake fahimtar hakan Baaba, kaman kuma mutanen gidan ba su ɗauki ma'aikatan su da muhimmanci ba" Ta ɗan juya kai cikin manyanta tace "ko kuma ita Afeefar ce ba su ɗauke ta mutum ba ba" Ajiyar zuciya ya sauƙe daga nan bai sake magana ba itama haka har suka isa gida, ta sauka kenan yana shirin ƙarasar da motan parking space ta juyo ta kira shi "Alhj ƙarami Don Allah idan za ka koma da dare ko ban bi ka ba zan baka kunun gyaɗa ka kai mata kila ta iya shan shi" Ya amsa da "Toh Baaba Allah ya kaimu dare ɗin" Ya ƙarasa da motan yayi parking kan ya nufi cikin gidan shi ma don bashi da aiki da safen sai dare za shi asibitin ya kwana, Salim ne ya fitar dashi dole. Da misalin ƙarfe bakwai na dare ya fito a shirye tsaf cikin kananun kaya da suka amshi kalarshi na baƙi, skin ɗin shi da yake kalkalewa tamkar mace sai shining yake don shi mutum ne mai tsananin tsafta, hannun shi rike da ninkakken labcoat ɗin shi, mahaifiyarshi Hajiya Amina da ke zaune cikin kujera ta ɗaga kai ta kalleshi "An fito kenan bokan Turai?" Yayi murmushi yana furta "Eh umma zan fara bi gidan su saleem akwai patient da zan duba kan na wuce asibitin" "A'ah ko dai wacce Baaba jummai ke ta jajenta tun safe?" "Ita fa Umma da safe mun fita kina bacci, ko da na dawo ban leƙo ba ashe Baaba kam tayi ta baki labarin Afeefah" Tana murmushi tace "Ai ina ga zuwa yanzu kowa ya san labarinta a gidan nan, Allah ubangiji ya bata lafiya. Sai ka leƙa kitchen ta yi mata kunu da ferfesu ka karɓa ka tafi mata dashi" Yayi murmushi kan ya amsa yana nufan kitchen ɗin baabar tana side ɗin su bai neme ta bane saboda ba gida zai dawo ba daga chan asibiti zai wuce shiyasa ma bai ba kanshi wahalar neman ta ba don sai yayi mata dogon bayani da kyar ta fahimce shi, kwando ne mai kyau da tsari ta shirya mata komai ciki, ya dauka kawai ya fito yana yi wa Ummarshi sallama take sanar mishi Abban su yace ta sanar mishi lallai lallai yana son ganinshi da safe saboda kullum a saɓani suke. Ko da ya isa gidan su saleem a mota ya cigaba da zama yana tunanin yadda zai nemi iso don bai ga gilmawan kowa ba, sai time yake dubawa ganin zai iya makara ya sa ya sauka ya nufi mudi dake zaune bakin gate da iliya. "Assalamu Alaikum warahmatullah" Yayi musu sallamar yana sake miƙa mishi hannu duk da sun gaisa Shigowar shi "Don Allah ku dan yi haƙuri zan shiga lokacin aikin ku, Afeefah nake son gani ko za ka min iso?" Shiru suka yi cikin tunanin wacece ma Afeefah a gidan, a tare suka tuna ta sai suka kalli juna suna zazzaro ido, mudi ya ce "A'a malam sai dai ko in nema maka Talatuwa ta maka iso amma mu kam magana ma da wacce ka ambata ya haramta tsakanin mu har Abada" Ya ƙarasa cikin yanayin jimami da tabbatarwa iliya ma na gyaɗa kai tabbacin hakan ne. "Magana ya taɓa haramtuwa tsakanin musulmi da musulmi kuwa Malam mai gadi?" Yayi maganan yana ɗan dariyar yadda suke reacting. "Kai dai in ana sallah ba'a magana" Iliya ya faɗa, tuni mudi ya nufi ciki ta baya ya bi ya tsaya daga kofan mashigan kitchen ɗin "Talatuwa akwai wadda ke neman iso wurin yarinyar nan mai wanke-wanke zo ki ji da shi" Sameera da ke shigowa kitchen ɗin ta ɗan yi jimmm kan tace "Talatuwa ci gaba da aikin bari na je" Da kallo Talatuwa ta bi ta har ta ɓace, sai da ta koma ɗaki ta dubi kanta ta kuma ƙara turare kan ta fito ta nufi waje, Sulaiman na ta bugar cikinsu don ya ji dalilin rashin mata magana kuma wai na har abada dole ya sa suka shiga bashi labarin abin da saleem yayi musu, Sossai Sulaiman ke dariya... Tahowar Sameera ta wani zuba mishi idanu tana tsintar kanta da murmushi. Kallon farko da ta mishi ya tafi da imaninta, ya shiga ranta fiye da yadda tarin samarin da suke bibiyar ta, a yanzu da ta ci karo da shi yana dariyar nan kuma sai taji tana narkewa, zuciyarta na wani irin macewa a kanshi, ganinta ya sa ya tsagaita dariyar shi, ta shiga gaishe shi ya amsa yana murmushi "Whats so funny haka Dr.?" "Ki bari kawai ni da su mudi ne, zan iya shiga?" Ta ɗan yi farrr "Sauri kake haka?" Ya ɗan duba time a agogon dake ɗaure bisa tsintsiyar hannun shi "Kusan hakan don kaman na shiga lokacin aikina" Ya ƙarasa yana nufar mota, ta bishi suka jera. "Ai ma kuna ƙoƙari SLT nake karantawa amma ji nake kaman na gudu bare likitance da aikinshi" Ya ɗan yi dariya bai ce komai ba, ta tsaya tana kallonshi har ya buɗe booth ya ɗauki kyakyawar basjet da Baaba jummai ta shirya mata kunu da ferfesu ɗin kayan ciki da suka nuna suka yi tuɓus cike da kayan kamshi, ganin basket ɗin sai da ya ba Sameera haushi amma ta danne, ta sake ganin ƙatuwar leda sai zuciyarta ya shiga tambayarta Anya alaƙar nan na likita da marar lafiya ne ko akwai abin da bata sani ba? Amma me Afeefah take dashi da guy irin Sulaiman zai so ta? Dukda haka zuciyarta bai huta da bugun tara-tara ba, kar dai ta faɗa soyayyar abin da ba za ta samu ba, ji tayi bata da ƙwarin gwiwar bin shi don tabbas matukar ta bishi ta fahimci akwai alaqa tsakaninsu zuciyarta zai iya bugawa ko ta shaƙe yarinyar har lahira, ba za ta iya bin shi ba sam bata da ƙwarin gwiwar. Ta manta cewa kwata-kwata ma yau ne ta fara ganinshi har da zaƙewa haka, wayar ƙarya ta ƙirƙira ya ɗan kalleta "Ka je Dr zan sameka" Tana kai nan ta juya tana cigaba da magana a ƙarya, shi kam bai damu ba ya nufi ɗakin Afeefah ɗin a kan varender ya tsaya yayi knocking, a jiran da ya ɗan yi ya fahimci maza ne cikin ainihin Boys quaters ɗin don ga wani murya na waya, kuma shine aka ajiye mace tare da su? Sam tsarin bai mishi ba... Anan ne kuma ya shiga tuna hirar su iliya sai ya fahimci saleem yayi hakan ne don ya bata kariya Dukda haka shi abin bai burge shi ba, ya juya ya kalli main building na gidan, yanzu duk girman gidan nan a ce babu inda za'a ajiye Afeefah sai cikin maza? Kimtatar lokaci yayi daga knocking da sallamar shi zuwa yanzu kan ya tura kofan ya shiga da wani sallama again, ta lallaɓa ta tashi zaune ta sanya hijabi tana jingine da gini ƙafafunta na cikin bargo "Sannu da zuwa Dr" Ta faɗa cikin sassanyar muryarta da ya ƙara ƙasa sossai. "Sannu Afeefah ya jikin dai?" Ya faɗa yana ajiye abubuwan hannunshi "Da sauƙi" Plate na safen nan ya ƙara gani a yadda aka ajiye da safe, wani tunani ne ya darsu a ranshi hakan ya sa ya miƙa hannu ya buɗe ga mamakin shi abincin nan na safe ne still zaune cikin plate ɗin, bata ci ba don ko da Talatuwa ta shigo ta duba ta ta ɗauka ta tafi da shi don ta kawo mata wani mommy ta koro ta akan ba za su yi almubazzaranci ba sai dai ta cinye shi kan a saka mata wani. "Afeefah tun safe baki ci komai ba?" Da ɗan tausayi haɗe da zafi yayi maganan ranshi na sosuwa kwarai. Ta Yi shiru "Ina za ki samu ƙarfin jiki idan ba kya cin komai? Ai ko mai azumi zuwa yanzu dai ya sha ruwa" Tsam ya miƙe ya nufi bayin ta, ta lumshe ido bayan ya shige chan sai gashi ya fito da bowl haɗe da brush ya bata, ruwan goran da ya shigo dasu ya buɗe bakin ɗaya ya dinga zuba mata tana wanke bakin sai da ta gama tsaf ya mayar yaje ya zubar, ya dawo ya tsuguna ya saka mata peppersoup ɗin da kunun ya ajiye mata a kan kafafunta ɗayar hannunta na hagu ya miƙa mata kofin kunun ta karɓa ta riƙe idanunta na kallon cikin bowl na psoup ɗin, sai turiri da kamshi yake fitarwa. "Oya ci yanzun nan, ko in baki da kaina?" Ta girgiza kai ta sanya hannu ta dauki spoon ɗin ta shiga sha, da kaɗan da kaɗan yana matsa mata har ta sha dayawa ta sha kunun kuwa sossai, fruits da ya sayo mata ya kara mata da shi. Ta marairaice "Zan yi amai fa idan na ci, cikina ya cika" "kin manta kina tare da likita? Ai aman ma tsorona yake ji Harara ɗaya tak zan mishi ya koma" Ta saki murmushi karo na farko da har hakwaranta suka bayyana, ta sanya hannu ta karɓi ayaban da ya bare mata. Magungunan ta ya duba ya haɗa Allura yayi mata a canular tana ta wash wash ya ce "Wato ɗazu ma saboda bakya hayyacinki ne kika manta da raki ko?" Ta duƙar da kai, wayanta ne yayi haske ya ɗauko ya duba "Saleemullah ne yayi miki saƙo in karanta miki?" Ta girgiza kai alamun A'a. "Zan duba anjima" Ya gyaɗa kai ya shiga Phone ya sanya Layin shi yayi flashing kan yayi saving da "Dr. Sulaiman" "karɓi, zan zo gobe da safe duk abin da kika ji kina so ko sha'awa just give me a call za ki samu kin ji?" "Toh Dr na gode" Yayi saurin cewa "Yanzu kam na wuce wannan matsayin tunda har jinyarki kika saka ni a bati" Tayi dariya kuma da gaskiyar shi don ta mugun samun ƙwarin jiki, da Allah bai turo mata shi ba haka za ta kwana don ba zata iya cin abincin safen ba. Sallama yayi mata ya fice don ya makara yau kam ainun. Sameera da ke tsaye jikin Window tun ɗazu ta ƙura mishi ido tana jin zafi a ranta, idan ta kimtata daidai mintunanshi Arba'in da biyar a ɗakin yarinyar me ya ajiye shi haka? Har zafi zafi take ji a idanunta shi kam da bai san ma tana yi ba tuni ya shiga motar shi ya bar gidan. 🖤Gureenjoh🖤 HAIHUWA DA HANJI (A True life story) Fatima Muhammad Gurin (Gureenjoh) Wattpad-Gureenjo6763 Arewabooks-Gureenjoh *FREE BOOK* *015* Ta ɓangaren Afeefah Dr. Na tafiya ta janyo wayan, number Dr. Sulaiman shi ne number na biyu da ya shiga wayanta murmushi ta ɗan yi bayan ta buɗe sakon Saleem. Kusan saƙon shin na ashirin da wani abu kenan a ranar. "Ya jikin? Kin ji sauƙi? Kin ci abinci? Don Allah kar ki zauna da yunwa ki ci ko kaɗan ne, ko akwai abin da kike so in sa a kawo miki?" Saƙonnin kenan masu dauke da kulawa. A yanzu ma emphasizing yake akan ta ci wani abu cike da damuwa ƙarara a kalaman nashi duk ya damu, rubutu ta fara a hankali "Na Ci abinci kuma na ji sauƙi sossai ka kwantar da hankalinka ka ji Ya Saleem?" Numfashi mai nauyi ya sauƙe a sadda saƙon ya riskeshi matsalar shi ko ya baro Maiduguri ya dawo Kaduna a yau bashi da damar bata kulawa yadda ya dace hakan na damun zuciyarshi ƙwarai da gaske. "Alhamdulillah! Yanzu ni ma zan iya saka wani abu a baki na, na gode Afeefah. Ki kular min da kan ki sossai in akwai wani damuwa kar ki yi ƙasa a gwiwa wurin sanar min" Hawaye ne suka cika idanunta, me yasa zuciyarta ba za ta karye a kan saleem ba? Shi ne mutum na biyu da ya karɓe ta a yadda take, bai damu da maganganun mutane ba, ya ba ta kariya daga cutarwa ya ɗauko ta ɗaga kan titi ya kawo ta gidan su, yana iya ƙoƙarin shi wurin ganin bata zubar da hawaye ba, bata san da me za ta saka mishi ba bata ma da abin saka mishin da ya wuce Adu'a, har ranta take jin duk abin da mahaifiyarshi da ƙannenshi za su yi mata in har akwai hakkinta ta yafe musu ba za ta taɓa rike su ba saboda salim ya wuce wannan gaɓa a rayuwarta. "Ka ci sossai har da sauran kaso na, sai da safe" Tana kai nan ta kife wayar tare da kwanciya don da Talatuwa ta shigo ɗazu ta roƙe ta ta kawo mata ruwan dumi tayi alwala, da alwalar tayi ta sallolinta daga zauna saboda jiri da baya barin ta ta tashi. Ta ɓangaren Sameera wani tsanar Afeefar ya sake cika zuciyarta, tunanin matakin da za ta ɗauka a kanta take yi, ko ta je tayiwa Afeefar gargaɗi akan kula Dr ne? Wani zuciyar yace yanzu duk abin da fushi ya dibe ki kika yi mata tsautsayi ya faɗa kanki a bata da lafiyan nan ai kin kaɗe, gwara ta warke first a haka dai da nauyin zuciya ta kwanta tana ta juye-juye cike da haushi da tsanar Afeefah da tayi sanadiyar kasa baccinta a daren. Kaman yadda Dr. Sulaiman ya yi alƙawari bayan ya tashi aiki da safen wanka kawai yayi ko hutawa bai yi ba ya ɗauki Baaba jummai don yana so ta yini wa Afeefar kila jikin ya sake ƙarfi idan ta ga mutum kusa da ita, sam baya so abin da ya faru jiya ya faru yau hakan ma ya sa yayiwa Baaban umurnin shirya mata duk wani abu da ta san bakin marar lafiya zai so da basket mai girma suka nufi gidan, ba su wani nemi iso ba suka zagaya zuwa sashen Boys quaters ɗin ya bar Baaba ta soma shiga. Afeefar ta ji ƙarfin jikin nata sossai musamman da ta samu baccin dare mai nauyin gaske, ta samu ta lallaɓa ta watsa ruwa ta ɗan kimtsa ɗakin tana sanye da peach abaya ta ɗaura gyalen a kanta, ganin Baaba ya sa farin cikinta bayyanuwa ainun, Baaba ma tana murmushi take cewa "Ah jiki ya yi kyau Alhamdulillah" "Sannu da zuwa Baaba" "Sannu Afeefah, ya jikin dai? Kin ga kan gaisuwar nan bari na shigo da Alhj ƙarami ya miki alluranki yana sauri zai je ya kwanta idan ba haka ba yanzu za ki ga ya kama ciwon kai da baya ƙarewa ta daaɗi" Afeefah murmushi kawai tayi Baaba ta fice seconds kaɗan sai ga su, Afeefar ta warware gyalen ta ta yafa bisa kanta, babu hula a kan hakan ya sa tsantsin gashinta ke ta zamar da gyalen tana gyarawa, gaishe shi ta shiga yi yana amsawa idanunshi na a kanta yana yaba yadda jikin ya fara kyau, Alluran ya haɗa yayi mata yau kam ma rakin ya fi na jiya, don akwai pcm kuma babu ruwan diluting hakan ya sa yayi mata a hankali yana yi mata sannu don zafin shi. Bai jima sossai ba ya tafi ya bar su da Baaba da ta zage ta ƙarasa gyaran ɗakin ya fita fess ta bata abinci tana ci suna 'yar hira bayan ta gama ma ta miƙe kwance suna cigaba da hirarsu tun tana amsawa baaban har bacci yayi awon gaba da ita. Shi Sulaiman yana isa gida ya ga Abbanshi tsaye suna magana da mai gadi, idanunshi ya ɗan runtse gabanshi na ɗan faɗuwa yau dai Abba ya kama shi, bai so ya dawo ya haɗu da Abban ba Dukda Umma ta gayamishi Abban na son ganinshi ya dai san tatsuniyar gizo bata wuce ta koki kuma shi kaman har yanzu bai shirya ba, haka dai ya sauƙa yana ɗan shafa kai ya matso su suka sake gaisawa da mai gadin a lokacin sun gama magana da Abban ya juya ya wuce. "Za ka shafa kai ai Sulaiman, wai Hausawa suka ce in kere na yawo zabo na yawo watarana dole a haɗu" "Barka da safiya Abba" Yayi gaisuwan a kunyace yana yar dariyar maganan Abban. "Barka dai Sulaiman ya aikin?" "Alhamdulillah Abba" "Toh ina magananmu ta kwana? Ka dai san na gama ɗaga maka ƙafa ko? Na fa gaji da ciyar da tuzuru don ka fi ƙarfin gauro" Abban na murmushi ya ƙarasa maganan Sulaiman Dariya yayi yace "Soon Abba in shaa Allah" "bari na gaji da Soon ɗin nan naka za ka sha mamaki, dama akwai yaran abokai da dangi da duk na yarda na kuma gamsu da nasaba da tarbiyar su sai dai ka ji an saka maka rana, kar ka ga ina murmushi Sulaiman wannan ne last chance ɗinka, wai kai ko kunya baka ji? Kannenka duk sun tara 'ya'ya maza da mata kana zaune abin ka?" Har lokacin murmushi yake, ya matukar sanin mahaifinshi Alhj Abdulrasheed mutum ne mai saukin kai da sauƙin hali Dukda tarin kudin da Allah ya bashi, ɗan kasuwa ne da har yanzu bai daina nema ba daga shi har yaranshi suna da sauƙin hali da kyautata mu'amala da duk wanda hakan ya haɗa su. "In shaa Allahu Abba za ka ji alkhairi i promise" "I hope so, yanzu kake dawowa daga aikin kenan?" "A'a Abba, na dawo da wuri na ɗan je na duba wata patient ɗina ne a gida na ba ta medication" "Toh yayi kyau, a je a huta Allah ya taimaka" Ya amsa da Ameen yana jera wa mahaifin nashi adu'ar ƙara girma da lafiya ya wuce ɗaki, haka kawai yake tsintar fuskar Afeefah a idanunshi idanunta, murmushinta da ma sassanyar muryarta na dawo mishi kaman a yanzu take yi mishi, lumshe ido yayi yana sauke ajiyar zuciya... Kaman wasa fa sabo ya fara shiga tsakaninsu da Dr. Sulaiman kachokan yake bata dukkan kulawar shi ya kan zo kullum sau biyo har saida duka alluran ta suka ƙare, kuma bai taɓa shigowa hannu banza ba har ta kan rasa waye ya fi wani damuwa da ita tsakanin shi da saleem da bai taɓa hutawa da yi mata saƙo ba, ko da ta samu sauƙi ta komawa aikinta sai Sulaiman ya cigaba da ƙiran ta tun suna gaisawa kawai su yi sallama ya fara jan ta da hira da wasa. Yau tun safe jikinta ke a matuƙar mace, saƙon saleem ya shigar da ita rudani da damuwa marar misaltuwa Dukda ta tsammaci hakan sai dai ya daketa fiye da zato. Sallar asuba ta farka tana buɗe idanunta ta sauƙa tayi alwala ta zo ta gabatar da shafa'i da wutiri kan ta miƙa sallah, tana idarwa ta janyo wayan don karatu yadda ta saba sai ta ga pending message, buɗewa tayi ta ga ƙarfe 2 da 'yan mintuna gabanta ne ya ɗan faɗi me yasa saleem zai mata saƙo tsakiyar dare? Composing kanta tayi ta buɗe tana karantawa hawaye na silalo mata "Afeefah na san a lokacin da za ki ga wannan duniyarki za ta sake shiga rudani fiye da yadda take ciki a yanzu, na san tsoro zai mamaye zuciyarki, na san za ki yi tunanin anya saleem na cikin hankalinshi kuwa ya turo wannan saƙo? Toh duk lafiya ta ƙalau kuma ina cikin hayyacina hasali ma tunani da matsuwar zuciya akan fallasa sirrin ta su suka hana ni bacci har kawo wannan lokaci, Afeefah na kasa hana zuciyata ƙaunarki... Zuciyata ta kamu da Soyayyar ki ba na wasa ba, wallahi Soyayyata a gareki gaskiya ce, kuma ta ginu ne daga tushen tausayi Afeefah ina ƙaunarki fiye da yadda zan furta miki" Kuka kawai ta fashe dashi tana haɗa kanta da gwiwa, wani sabon al'amari ne kuma ke shirin shigowa rayuwarta? A sadda take karanta sakon Saleem duk wani tsika na jikinta sai da ya tashi, zuciyarta kaman zai Faso kirjinta ya fito Dukda ta jima da tsammatar hakan sai dai bata kawo hakan kusa ba, ba tsoron ta soyayyar shi ba tsoronta danginshi ta ina za ta fara son saleem? Ta yaya? Ta san saleem duk inda mace take neman nagartaccen namiji ya kai har ma ya wuce abin tambayar mahaifiyarshi da 'yan uwanshi za su karɓi uzurinshi? Ta Tabbatar muddin suka ji cewa salim na son ta zamanta a gidan ya zo ƙarshe kenan to in sun kore ta ina zata je? Ko da ta koshi da kukan ta fito ta ƙarewa gidan kallo sai taji ma har wacece ita da namiji kaman saleem zai so ta? Har wacece ita da za ta yi mafarkin rayuwa da saleem? Ai ko da girgiza kanya ta fi magarya zaƙi. Jiki a sabule ta gama dukkanin ayyukan ta, ko da ta dawo ɗakin ta sake samun sabon saƙon saleem. "Afeefah na san na saka ki a rudani sai dai nima na rasa mafita ne, wallahi ban san sadda soyayyar ki ta samu matsuguni haka a zuciyata ba, ba ni da iko da ita bare har in hana ta. Don Allah kar ki yi kuka kuma kar ki firgita idan ba kya so ba zan tilasta ki ba don wallahi na fi kaunar farin cikinki da nawa farin cikin, kar wannan dalili ya sa ki ja baya da ni kawai na sauƙe wani nauyi ne da nake jin ya zame min dole na sauƙe, ina sake sanar da ke cewa Na so ki jiya, na so ki yau, zan cigaba kuma da son ki har zuwa gobe sannan zan cigaba da son ki kowace rana" Numfashi mai nauyi ta sauƙe hannunta har rawa yake, hawaye kuwa ya fi pampo zuba a fuskanta, ita dai da bad luck aka halliceta mugun tabo da shaidar ta zai cigaba da bibiyar ta har abada, a yau anan ba wani ne ya mutu ba amma tambarinta shi ya ja mata tsanar da ba zai taɓa sanyawa mommy ta amince da ita a matsayin surka ba ko tana mutuwa tana farkawa kuwa. Bata san yadda yake ji a ranshi ba amma ta san abin da zai hana shi sukuni haka babba ne, ba za ta bari salim yayi kuka saboda ita ba don haka a hankali ta rubuta "Allah ya zaɓa mana abin da ya fi alkhairi" Lumshe ido yayi daga ɓangaren shi, shi karan kanshi tsoron yake ji, amma ya zai yi? Kalamai ya cigaba da mata na kwantar da hankali gabaɗaya yinin, ganin ya damu sai ta danne nata damuwar ta nuna mishi bata da matsalar komai kuma a shirye take da duk abin da zai je ya dawo, ta san bata da wannan ƙwarin gwiwar amma da shi kila komai ya zo da sauƙi. Washegari da yamma tana zaune tana karatun alqur'ani kawai ta ga saƙon shi "Hey dear zan dawo gobe, me kike so na taho miki da shi?" Ta karanta text message ɗin ya fi sau uku zuciyarta haka kawai ya shiga bugawa amma ta dake ta rubuta "Ka fi kowa sanin abin da ya fi cacanta da ni, duk abin da ka kawo ba zan ƙi farin ciki ba" Murmushi mai kyau ya saki, yana Fatan kasantuwar alaƙarsu na har Abada yana fata da Adu'a akan muddin ya fito fili komai ya zo mishi da sauƙi don babu yadda ya iya da abin da zuciya take so. A Washegarin duk iyalan gidan suka shiga shirin tarbar breadwinner ɗin su, hidima kawai ake don a wannan karo ya ɗan jima bai zo ba, dab la'asar ta gama wanke-wanke tana shirin shiga wanka ta ji wayanta na ringing, ta san Sulaiman ne don shi kaɗai yake kiran ta sai kuma saleem da yake mata text message, dagawa tayi tare da sallama ta shiga gaishe shi, ya amsa cike da wasa kaman yadda yake mata tamkar 'yar baby ya ɗauke ta. "Yau dai haka kawai na ji ina son ganinki har mafarkinki na yi fa da na yi baccin rana, zan tafi office da yamman nan idan kin ba ni dama in biyo in kalle ki ko kaɗan?" Ta ɗan sauke numfashi a ɓoye a hankali tace "Ni na isa hana ka?" Da ɗan murmushi yace "A'a ai na zaci za'a yi min rowan wannan beautiful and innocent face ɗin ne" Tace hmmm, wani zuciyar na ce mata kila fa shima in da ya san wacece ita ba zai raɓeta ba. "Sai ka zo, a gaisar min da Baaba please" "Banda ummana?" Yayi maganan a hankali, tayi murmushi "har da ita fa Dr. Da ma kowa da kowa" "Toh wa zan ce mata tana gaisheta?" "Afeefah mana?" Ta faɗa tana 'yar dariya murya a karye, shi ma murmushi kawai yayi ya yanke call ɗin. Wankanta ta shiga a gaban madubi ta tsaya tana ƙarewa kanta kallo, sossai ta ƙara ganin chanzawarta ba'a tsawo ba don dama chan ita ɗin doguwar mace ce, sai dai ta ɗan kara kauri saɓanin da da take lange-lange kuma fatar ta ya kara wani irin kyau da sheki, mutane dayawa su kan yabi kyaun fatarta musamman a zamanta da Aunty zee amma bata taɓa yarda fatar mai kyau bane kaman yanzu, ta buɗe sossai daga ƙasa sai dai saman babu wani auki tsarin jikin sai ya bata wannan figuren da ake cewa coca-cola, a sadda take Dutsen-wai bata taɓa kawo ko a mafarki za ta auru ba amma da ta dawo Anchau Dukda jita-jitar da ake yadawa a kanta hakan bai hana wasu tararta da sunan So ba amsar ta dai karatu ne a gabanta, ta kuma san ko ta amince da wuya ne a haifi da mai ido musamman ga 'yan uwa da abokan arzikin wanda za ta amincewar, a yanzu kuwa da babu halin karatun muddin ta cigaba da zama a gidan tana jin za ta so matsawa wani environment ɗin inda za ta samu so a yadda take kuma a bata rayuwa ingantacciya, amma Saleem shi ne namijin da zuciyarta ta fara aminta dashi don ya yi mata abin da kuɗi ko godiya ba za su taɓa biyan shi ba. Tana wanka haka kawai tana hawaye, tana ji a ranta matuƙar komai ya bayyana kwaɓarsu za ta yi ruwa ba na wasa ba, kuma wa'adin zamanta a gidan ya ƙare, amma in ta saurari Sulaiman fa? Sulaiman bai san asalin ta ba, bai san tarihi da mugun tabon ta ba idan ya sani kila shi ma iyayenshi ba za su taɓa karɓar ta ba. Da wannan tunani da damuwar ta fito daga wankan. Man shafawar da Sulaiman ne ya kawo mata haɗe da wasu dogayen riguna inda yake ce mata babu abin da ke karbarta kaman dogayen riguna ko don bai taɓa ganinta da lace ko atampha bane amma tana matukar tafiya da tunanin shi in ta saka su shi ta shafa, ta ɗauki wani maroon Abaya da ya sake fito da kyaun skin ɗinta cikinsu ta saka, ta ɗan fesa turare tare da man leɓe kaɗan, mayafi ta yafa daidai Sulaiman na ƙara kiranta a kan ya zo. Shi kuwa Sulaiman a sadda ya gama shiryawa ya fito parlorn ya ci karo da mahaifiyarshi da ƙannenshi. "Sai ina Ya Sulaiman?" Ɗayar ta faɗa. "Ina ruwan ki? Sa ido...." Ya faɗa yana hararanta. Wacce suke tsananin kama da wacce suka yi maganan da farko tace "Sana'ar banza ba, ai yaya ka fita sabgar fa'iza ta cika saka ido. In zo in raka ka ne?" "Kema bana so gulmatu" Dariya suka sheke da shi ganin yadda ya ke hararinsu. Tsaki ya ja "Umma na tafi" "A gaishe min da surkar tawa" Narkewa yayi "umma wai har da ke a biye wa waennan yaran?" Ta Yi dariya tana cewa "Sai dai ka dawo" Ya fice abin shi a jikin mota ya tsaya yana kokarin shiga sai ga Fauza ta miƙa mishi wani leda wai in ji Umma ya kai mata, yayi murmushi ya karɓa kawai bai ce komai ba. Gidansu akwai sauƙin hali da haɗin kai shi ne babba, yana da imediate kanwa da tayi aure sai wani namiji kafin twins ɗin nan mata biyu, mahaifinshi fitaccen ɗan kasuwa ne inda mahaifiyarshi ke aiki da federal government, ba su taɓa raina talaka ko ya yake musamman Sulaiman da shi ko na kasa da shi ya kan girmama, babu mai cewa ga wani tambari nashi ko hali marar kyau Dukda kowani mutum tara yake bai cika goma ba. Sai da ya biya ya kara mata sayayya akan na Umma kaman koyaushe matukar zai je wurinta bai taɓa zuwa hannu banza ba ya nufi gidan, bayan yayi parking ya ƙira ta, Bata kai ga fitowa ba aka wangale Gate ɗin gidan Motar Ryan ta kutso kai ciki a hankali... 🖤Gureenjoh🖤 HAIHUWA DA HANJI (A True life story) Fatima Muhammad Gurin (Gureenjoh) Wattpad-Gureenjo6763 Arewabooks-Gureenjoh *FREE BOOK* *016* Kaman yadda ƙa'idarsa take ba ya hanzari ko gaggawa a koma menene sai ya sha Ƙamshin nan dai wane saraki haka a yanzu ma, sai da saleem dake sanye da khakin sojoji full 6/6 don hatta agogon da Ke ɗaure a tsintsiyar hannunshi da ƙatuwar backpack na bayanshi duk na sojojin ne ya sauƙo kan ya buɗe motar ya sanyo jiki. Yau sanye yake da wata farar kaftan da aka yi wa ɗinkin zamani ya matuƙar zauna mishi kuma farar fatarshi ya ƙara haskaka, daga takalmi har agogon fatar dake ɗaure a tsintsiyar hannunshi farare ne, kanshi babu hula sai kwantaccen gashin shi na ainihin Fulanin asali da ke sheƙi, ganin Dr Sulaiman ya ɗan ba saleem mamaki shi ma kuma Sulaiman ganin su ya sa ya taso daga jikin motar shi ya isko su Saleem ya fara miƙawa hannu fuska a sake suka gaisa kan ya miƙawa Ryan shi ma ya karɓa suka gaisa cikin 'yar nuna sanayya amma fuskar nan kadaran hadaran. Magana suka cigaba da yi da salim da ta shafi Lafiyar Afeefah shi dai Rayyan tun da suka gaisa ya zaro wayanshi ya kuma mayar da hankalinshi kai don hirarsu ba huruminshi bane. Tun da ta hango su gabanta ya yanke ya faɗi, abin da za ta cewa saleem ya kawo Sulaiman gidan ke ta kai komo a ranta, tafiya take tamkar hawainiya saboda bugun zuciya, su ukun duka kwarjininsu ya wani rufe ta tun kan ta iso inda su ke, Zaratan samarin masu jini a jika cikakkun maza kuma kamilallu, kowanne kuma gwani ne a nashi fagen kyaun da kamala. Ji ta yi kafafunta ba za su iya daukar ta ba a sadda mai fararen kayan ya ɗago idanu suka shige zuruf cikin nata. "Rayyan!" Sunan ya yi ringing da matukar ƙarfi a kwakwalwarta, wannan idanu ba za ta taɓa manta shi ba tuni ya mayar da kanshi kan wayanshi amma ita ta daskare ta kasa motsa kowani gaɓa na jikinta, idanunshi sun fi yanayi da na maguna kwayar wani surkin kala ne da kan rikita lissafin duk wadda ya zubawa su, ƙasan lid ɗin tamkar an zana mishi kwalli zirrr baƙi sidik hakan sai ya kara saka idanun zama na daban da sauran mutane, idan idanun suna duƙe za ka zaci a rufe suke saboda tsawon lashes ɗin sa ga su baƙake kaman gashin kansa da na girarsa. "Afeefah!!" Saleem ya faɗa da ɗan karfi a karo na uku, firgigit tayi ta dawo hayyacinta. "Ƙaraso mana kin tsaya daga chan" Bai sake magana ba har ta ƙaraso inda suke daga shi har Sulaiman idanunsu na a kanta. Da kyar ta iya buɗe baki tace "Sannu da isowa Ya Saleem" "yauwa Afeefah" "Ina yini?" Kai kawai ya ɗan gyaɗa mata hakan ya sanar da ita cewa lokacin da ya kamata yayi magana da ita ya wuce. "Yaya Sulaiman ina yini?" Muryarta da ya karye ya ƙara sanyaya yana fitowa a slow, ɗago ido Ryan yayi ya kalleta daidai tana ce mishi shima Ina yini? Ya kau da kai kaman bai gane da shi take ba, daga shi har saleem sun fahimci chanzawar muryarta, shi Ryan kam ma mamaki ne fal ranshi don a yanzu abin da ya sa ya sake kallonta tuna abin da saleem ya gama faɗa mishi bayan ya ɗauko shi daga Airport wai son yarinyar nan yake, in ba janyowa kai raini ba shi bai ga abin ba ya tabbatar a auren ƙauye sun kusa ajiye irin ta. Tsaki ya ja a fili yana furta "Man we talk later!" Ya faɗa cikin muryarshi mai cike da ginshira sai Muryar ya bata tsoro ta tuna ranar da yake daka mata tsawa da hanzari ta ɗago idanu ta sake kallonshi, ya miƙawa Sulaiman tender fingers ɗin shi da kaman zai fidda jini don haske da taushi suka yi musabaha, yana kokarin buɗe mota idanunshi suka sake shige wa cikin nata, daga ita har shi suka yi saurin kawar da idanun ya shige ya ja ya bar gidan. Saleem ya dubi Sulaiman ya ce "Nima kaman zan shiga daga ciki jikina kaman an min duka" Sulaiman na murmushi yace "Ai dole, a huta gajiya mazan fama" Suka yi musabaha kan ya nufi ciki, ya zaci Afeefah ma za ta yi wa Sulaiman ɗin sallama ta biyo bayanshi sai ya ɗan waiga nan ya ga sun matsa jikin motar Sulaiman ɗin yana mata magana a hankali ita kuma tana dariya, tuni duk wani walwalar fuskarshi ta kau, ranshi ya shiga suya bai iya ya shiga main parlorn ba ya bi ta baya ya haye sashenshi, backpack ɗin kawai ya ajiye ko zama ya kasa yi ya dawo jikin Window yana kallonsu, kusan mintuna talatin suka yi suna hira kan ya ga Sulaiman ya buɗe mota ya fiddo wasu ledoji ya miƙa mata. "Ga shi umma wai na kawo miki" Tayi murmushi mai kyau cike da jin daaɗi tace "Allah sarki umma, ka yi mata godiya na ji daaɗi sossai Allah ubangiji ya kara girma da lafiya" Wayanshi ya zaro yana furta "Ko kuma ki yi mata da kan ki ba" Ido ta zaro kan ta yi magana ya shiga ƙiran ummar, bayan ta ɗaga da sallama ya ce "Ummar mu ga Afeefah tana so ta miki godiya" Kaman za ta nitse haka ta karɓa ta shiga gaisheta tana yi mata godiya, Albarka Ummar tayi ta sanya mata kan suka yi sallama ta miƙa mishi wayar tana ɗan tura baki na fushin yadda ya saka ta jin kunya, murmushi yayi "Kar ki sa na narke fah Afeefah" Tayi murmushi Ya miƙa mata wani leda mai girma da farko kin karɓa tayi sai dai da ya matsa ta karɓa ɗin tare da godiya suka yi sallama ta nufo ciki. Da hanzari Saleem ya ɗauko wayanshi ba ta ko kai ga shiga ɗakinta ba ta ga saƙon shi "Menene ke tsakani ki da Sulaiman?" Muƙut haka ta haɗiye wani miyau kaman yana gabanta, da sauri ta shige ɗakin ta ajiye ledar tare da zame mayafinta ta jefa kan katifa ta fara safa da marwa cikin tunanin amsar da za ta bashi, sam bata so yayi fushi da ita da kyar ta iya rubuta mishi "Babu kawai kyautatawa ce da suke min shi da ahalinshi" Shiru ba reply, ta san ba wai ya yarda bane kuma kila shirun nan da ya yi fushi yayi, ta kasa zaune ta kasa tsaye haka ta yi ta saƙe-saƙe ita kaɗai, ƙiran Magrib ne ya katse ta jiki a sanyaye ta shiga bayi tayo alwala ta zo ta gabatar da sallah ta zauna nan tana karatu. Sulaiman kasa zuwa office yayi haka kawai yake sake tariyo kallon da saleem ke yiwa Afeefah, ji yayi ko ya je office ba zai taɓuka komai ba yana buƙatar shawara da mahaifiyarshi don tamkar ƙawarshi haka take. "Wash Allah na!" Ya faɗa yana kwantar da kanshi a kan kafafunta, ta sa hannu ta shafa sumanshi "Ya dai likita?" "kawai gajiya ne umma" "faɗamin gaskiya ko dai kai da surkar tawa ne?" Ya ɗan yi shiru kan ya ce "Ina tunanin umma saleem na son Afeefah, ko dai ita bata sani ba ko kuma ta sani tana min wasa da hankali ne" "Saleem shi ne ɗan masu gidan da take aiki?" Kai ya gyaɗa mata "Kuma Baaba ta tabbatar min kaman yarinyar tana shan wahalan gidan aiki haka ne?" Nan ma ya gyaɗa kai fuskar shi babu walwala "Kaman saleem ɗin ne kawai yake taimaka mata, kuma kaman ba ta da kowa don dole ne kawai take zaune gidan" "Ka kwantar da hankalinka Sulaiman, kila ba soyayyar ba ce tsakaninsu sai kyautatawa don ya na tausayinta, kila kuma yana son ta ɗin amma yana tsoron bayyana mata don iyayenshi, zai ma iya yiwuwa ya sanar mata ɗin amma ta ƙi bashi haɗin kai don babu macen da za ta yi kuskuren jefa kanta inda ta san ba'a ƙaunarta ko kuma inda za ta sha wahala" Numfashi ya sauƙe "Umma haka kawai nake jin kaman ba zan sameta ba" "Ka cigaba da kyautata mata domin zuciya tana son mai kyautata mata, idan har matarka ce za ka aureta, ni ma zan so ka sameta don na tabbatar wacce ta iya mallake zuciyar My Son ba ƙaramar nagartaccciyar mace ba ce" Ya miƙe zaune yana murmushi "Umma za ki fara taya autocinki zolaya ta ko?" "Ai gaskiya ne sabon shiga, duk ka bar komai obvious sai gano ka muke yi dubi duk yadda ka ruɗe daga sanin tana da wani saurayin" Ta ƙarasa da dariya. "Duk ba za ku gane bane umma ni dai na yi nan" Yana ji tana cewa "Toh zo ka ganar da mu mana" Yayi murmushi kawai. Allah ya gani shi karan kanshi ba zai ce ga sadda ya fara jin son Afeefah a ranshi ba, kawai dai ya san ta yi mishi kyau ranar da ya fara ganinta, sanyin muryarta idan tayi magana sai yake jin tamkar ƙanƙara ake zuba mishi. Ko da ta bar asibitin bai wani sa hope ɗin sake ganinta ba amma daga ranar da ya je ya isketa cikin fitar hayyaci sai ya ji tamkar an soki zuciyarshi da mashi barin ma da ya gama fahimtar tana shan wahalar rayuwa a gidan, sannan ya san babban burin ta a rayuwa shi ne ta yi karatu ta zama wata public figure da za'a yi alfahari da ita, kaman tana da wani ciwo ne da take jin ba zai taɓa warkewa ba har sai ta yi nasara a duniyar ta, ba ya jin zai iya bar wa saleem ita za su buga wasa ne duk wanda ya iya allonsa ya wanke. A daren da misalin ƙarfe tara ya ƙira layinta, ta gama wanke-wanken dare kenan da yau yayi yawa sossai saboda abincin da aka yi kalolin daban-daban, sai duba wayan take ko za ta ga saƙon saleem don gabaɗaya ranta babu walwala, ko da suka haɗu ko kallonta bai yi ba kuma ta sake mishi saƙo babu reply. "Assalamu Alaikum warahmatullah" A natse ya amsa "Wa'alaikissalam gimbiyar mata" Tayi ignoring sunan da ya ƙiratan "Ka koma gida lafiya?" "Da an damu da ni ai da an neme ni, ni da ya zama dole na ba gashi na kira ba. Ya kike?" Har za tayi magana ya katse ta "Wait!! Kina lafiya ko? Ya na ji muryarki duk cike da damuwa da rashin Walwala ba yadda na bar ki ba?" Ta ɗan ja numfashi tana tafiya kwance daga zaunen da take jingine da gini. "Kaina ke ɗan ciwo" "Eyyaa so sorry, kina da ORS?" Ta girgiza kai tana amsawa da "A'a" "Ki sha pcm da safe zan zo in auna jinin ki sai in taho miki da ORS ɗin, ciwon kai bashi da daaɗi musamman ga ke da jininki sauƙa yake kuma kin san ya fi high BP hatsari" Idanu kawai ta runtse bata san me zata ce ba tunda ta riga ta yi suɓutar baki ta ce kanta na ciwo zuwa kam sai ya zo to kuma saleem da har yanzu bai sauko daga fushin ɗazu ba fa? "Kina ji na kuwa Afeefah?" "Eh ina ji, na ce da ma ka barshi in na yi bacci zai daina" "hmmm ke dai kawai in na zo ɗin zan ƙira ki, kwanta ki huta Allah ya baki lafiya" Yana kai nan ya katse wayan ba ya so ta hana shi zuwa haka tayi ta juye-juye har bacci ya sure ta. Washegari tana gama goge-goge ko ɗaki bata koma ba sai ga ƙiran shi, gate kawai ta wuce don ta karɓa da sauri kan saleem ya tashi ya ganta "Sannu da zuwa" "kin tashi lafiya?" Yayi tambayar yana ƙare mata kallo, ita kam ko me ta saka kyau take mishi "Alhamdulillah ya su umma?" "Umma na gaishe ki da jiki ta ce in miki sannu" "Na gode sossai" Leda ya fitar ta zare ido, ko kayan jiya bata buɗe ba saboda damuwar fushin saleem da ita yanzu kuma ya sake ciko leda? Shi kam ba ya gajiya ne? "Hidimarka na yawa a gareni Dr. Na kan rasa kalaman godiya a gareka, wani lokacin sai in ji tamkar ba na kyauta maka don ka fara ƙaunata tun ba ka san wacece ni ba! Ban san ya za ka karɓeni ba a duk ranar da wani ya tare ka ya ce maka Afeefah annoba ce!" Kallon bana fahimtar zantukan ki yake mata daidai saƙo ya shigo wayar ta sanin saleem ne ya sa dole ta buɗe tana ta ƙoƙarin haɗiye kukan dake zuwar mata "Ki sallame shi za mu yi magana" Ta ɗago ta kalli Sulaiman da har lokacin idanunshi ke kanta. "Zan shiga ciki za mu yi magana" "Saleem ɗin ne ya ce ki sallameni?" Ya faɗa cikin wata murya yana ƙara tsare ta da idanu. Ba Ta yi magana ba ta mayar da kanta ƙasa kawai. "Ya za ki saka ni a duhu kuma ki tafi ki bar ni ciki? Me kike nufi a tare ni a ce ke annoba ce? Mutum ya taɓa zama annoba ne Afeefah?" Muryar ta na rawa tace "Kwarai Dr. Sulaiman da za ka iya da ka yi tattaki zuwa Dutsen-wai ka tambayi wacece Afeefah kamal ina da tabbacin bayan nan ko mai sunana aka ƙira maka za ka gudu! Umma ta karɓe ni ne domin itama bata san wacece ni ba don babu uwar da za ta karɓeni matsayin surka muddin tana ƙaunar ɗan ta" Ranta zafi yake mata, tana maganar ne tana tuna mahaifiyar saleem da kyamatarsu gareta ta wani ɓangaren kuma bata ga laifinsu ba don ba laifi bane mutum ya kare abin da yake so. "Ka yi haƙuri ka tafi Dr. bana so sai ka zurfafa kasan ni wacece in karya maka zuciya, na tafi ciki" Tana kai nan ta nufi ciki ta bar shi tsaye, hawaye take zubarwa ba wai duk cikinsu babu mai nagartar aurenta bane sai dai tana ji babu inda za'a karɓeta matuƙar an san wacece ita! Taɓon nan da bata san mafari ba ba zai taɓa goguwa a tarihin ta ba, tabo ne mai raɗaɗi da har Abada za ta cigaba da rayuwa cikin gangar jikin da ruhi mai tarin buruka suka mutu... Da saleem ta ci karo a sadda ta shawo kwanar ɗakinta ido kawai ya zuba mata ko da ta zo bata tsaya ba kawai ta wuce shi yayi saurin shan gabanta. "Afeefah saboda Sulaiman kike ɓata rai da ni?" Hawaye take yi wadda ta kasa sarrafa su cikin rabuwar murya tace "Ba saboda shi bane yaya saleem" Ta sake yunkurin wucewa ya sake tare ta "Ban gane ba bayan ga idanunki nan suna zubar da kwallah Afeeefa?" Cikin Muryar kuka ta shiga cewa "Ina kuka ne saboda na gaji da yaudara ta da zuciyata ke yi na cewar zan samu farin ciki, ina zubar da hawayene saboda na farka daga mafarkin da bashi da tabbas" Shesheka ta ja tana kallon cikin idanunshi "Ka gaya min Yaya saleem a cikin ku biyu da waye zan dogara? Da Kai da mahaifiyarka ta yi Allah ya isa muddin ka yi min maganar da ta wuce ta minti ɗaya ko da Dr. Sulaiman da bai san wacece Afeefah ba?" Wuce shi kawai ta yi don ta san ba zai amsa ba saboda minti ɗayan ya riga ya wuce hakan ya kara rura wutar zuciyarta ƙarfin kukan ya ƙaru, jakar hannunshi ya bi ta har cikin ɗakin ya ajiye ya tsaya ya zuba mata idanu yana jin kukanta na sukan zuciyarshi, idanunshi suka sauya sossai tausayinta da ƙaunarta suka ninku a cikin ranshi. Samha da ke tsaye jikin pampo ta sake hanci da baki tana kallon su ta kwasa da gudun tsiya ta kamo hannun mommy "Mommy zo zo zo ki ganewa idanunki wallahi Ya Saleem ne ɗakin Mayyar chan..." Mommy har tana tripping garin sauri suka nufi bayan a lokacin suka hangi bayanshi ya fito ya nufi hanyar waje, duk su huɗu suka nufi ɗakin kowa da bala'in da ke cin shi a rai... 🖤Gureenjoh🖤 HAIHUWA DA HANJI (A True life story) Fatima Muhammad Gurin (Gureenjoh) Wattpad-Gureenjo6763 Arewabooks-Gureenjoh *FREE BOOK* *017* 18hours Earlier Kanta a ƙasa tun da Sulaiman ya fita daga gidan tana tsaye ne jikin taga tana kallonsu tun Shigowarshi da ma isowar su saleem da tafiyanshi bayan ya ba Afeefar Abu a leda, bata taɓa sanin haka so yake ba sai da ta faɗa komar Sulaiman zuciyarta yayi mata wani irin nauyi, tsananin haushin Afeefah take ji kaman ta samu bindiga ta harbeta kowa ya huta, a yanzu ma bata san hawaye na zuba mata ba sai da ta ji an dafa ta. Ɗago kai tayi ta kalli Samha sai ta duƙar da kan again tana share hawayen fuskarta "Sameera me ke damun ki haka? Menene ya sameki kike kuka?" "Babu Samha" "A'a Sameerah ina fa lura da ke kwana biyun nan duk kin chanza kaman ba ke ba, kullum kina cikin damuwa 'yar faɗan nan da kike biye ni muyi tayi duk yanzu bakya yi walwala ta kau daga fuskanki har mommy ɗazu maganan take yi, in baki faɗa min ba wa za ki faɗawa Sis?" Kuka kawai ta sakarwa samhar, sai da tayi mai isarta kan ta ɗago ta kalleta "Samha ko na faɗa ma ba ku da maganin damuwata" "Ko Adu'a muka taya ki ai mun taimakeki bare kila akwai shawarar da zan iya baki, idan ba kya son kowa ya sani ne ma i promise ba zan faɗawa kowa ba". "Samha na kamu da Soyayyar Dr. Sulaiman" Tsayuwa tayi tana tunanin waye Drn Sulaiman sai da yayi clicking a brain ɗinta kan ta yi saurin cewa "Wannan likitan dake zuwa duba Mayyar chan?" Kai ta gyaɗa a sanyaye "Samha kaman soyayya suke da ita" "Amma Sulaiman ɗin bai santa bane ba ko? Ina nufin bai san wacece ita ba rufe shi take kokarin yi ta nuna mishi ita 'yar gidan nan ce?" Samhar ta fada har yanzu tana mamaki, Afeefah ta kai Sulaiman ya ce yana so? "Da alama kam" "Toh me kika yanke?" Ta ɗago jajayen idanunta tace "Dole su rabu idan na cigaba da kallonsu tare zuciyata zai iya bindiga Samha, dole ko in sakata ta rabu da shi ko kuma in san hanyar da zan bi gidansu su san wacece ita! Ko yana sonta ai ba shi zai aurar da kanshi ba ko?" Kai Samha ke gyaɗa wa "Wannan haka yake, shawarar nan yayi kuma ki sameta ki ja mata warning mai girma ta tsaya matsayin ta" A hakan suka yanke don har ta kwanta tana tunanin yadda za ta yi da Afeefah da safe kuma tana tashi bacci wanka kawai tayi ta fito kaman an ce ta leƙa waje ta hanjeshi tsaye da ita, ko abinci bata ci ba ta zauna parlor tana jiran Afeefar ta dawo don ta lura abin nasu gaba yake, bata gama tunanin ba sai ga Samha da gudu ta ƙira su suka nufi ɗakin Afeefar... *** Tana zaune kanta haɗe da ƙafafunta tana aikin zub da hawaye kawai ta ji an banko ƙofan ɗakin, suka tsaya suna ƙarewa ɗakin kallo kan Sadiqa ta nufi wayanta da ke zaune gefenta "Kutt! Yaushe kika yi waya? Na dai tabbatar ba da ita kika zo gidannan ba" Kayakinta Samha take dagawa tana cewa "Mommy yau dai kam Yaya da kike yabo ya watsa miki ƙasa a idanu duk wa zai saya mata su bargo har da su heather in ba Yaya ba? Dubi ƙwalamar dake ɗakin nan? Mommy anya ba asirce shi tayi ba?" Ita dai tana tsaye tana kallonsu duk da zuciyarta da ke dukan sakwara ta kame bata firgice ba, Sameera ta je ta fusgo ledojin da Sulaiman ya kawo mata tana zazzage kayakin ciki idanunta cike da kwallah. "Shikenan wallahi tambaɗe mana take shirin yi a gida, wani namijin ne zai na kashewa mace kuɗi haka ba tare da ta bashi komai ba?" Sadiqa ce tayi maganan tana ganin turaruka da dogayen riguna masu tsada da mahaifiyar Sulaiman ta bata. Sameera ta katse ta "Ko dai asiri ta yi musu ba yaya sadiqa in tambaɗe wa ne kenan har da Yayanmu kalli wayan nan kalar text messages dake ciki na tsantsar soyayya don tsabar rashin kunya da nuna cewa ta isa dashi ma kin ga sunan shi gatsau tayi saving saleemullahi" A fili ta fara karantowa mommy wasu inda yake tabbatar mata da zai iya jurar komai a kanta kuma zai jajirce har sai ya ga sun samu cikar burin su na kasancewa karkashin inuwa daya. "Ya isa haka sadiqa" Mommy ta faɗa jiri na kwasarta ta samu wuri ta zauna, har Dishi Dishi take gani saboda yadda kanta ya sara ashe salim zai iya tsallake maganar ta? Yanzu idan da basu lura da wuri ba tayi amfani da wannan dama ta kashe mata shi fa? Da gaske maita na tafiya da aljanu? Ai kuma duk inda Aljanu suke akwai asiri kenan dai tun farko ma asiri ta mishi ta sa ya kawo ta matsuguninsu? "Lallai saleem! Ni yaron nan zai nunawa ɗan yau ne shi? A kan mace? Macen ma Mayya marar galihu da tushe haɗe da asali mai kyau? Allah ya isa na a banza ya ɗauke shi? Ni saleem...?" Sai ta kama hawaye, hankalin Afeefah ne ya tashi ganin mommyn na mishi hawaye bata son masifar hawayenta ya taɓa shi ko ta wani ɓangare da sauri ta isa gaban mommyn ta zube a kan gwiwowinta "Don Allah Hajiya ki yi haƙuri kar ki mishi kuka, wallahi yana jin maganarki yana kuma tsoron fushinki, Ni ce mai kuskure ni ce na nemi ya sayamin kar ki yi fushi da shi domin fushinki bala'i ne a tare da shi..." Tauuuu sadiqa ta ɗauke ta da mari "Kin san hakan amma kike hure masa kunne ya saɓa mata? Kin san abin da ɓacin rai daga gareshi zai iya ja mata?" Samha da ta janyo jakar da saleem ɗin ya shigo ya ajiye mata ta zazzage komai na ciki tana cewa "Wallahi yarinyar nan so take ta raba mu da ɗan uwanmu Mommy, kalli uwar tsarabar da ya kawo mata a ɓoye ko ke bai kawo miki irin hakan ba bare mu... Farraku take shirin yi mana daga karshe ta sa ya kora mu daga gidan nan" "ƙira min saleem sadiqa" Da wayan Afeefar ta ƙira shi, ringing ɗaya ya ɗaga a hankali ya kira sunanta sai ta duƙar da kai hawaye na gangaro mata jin muryarshi. "Yaya Salim Sadiqa ce Mommy ke son ganinka" Runtse ido yayi da ƙarfi gabanshi na faɗuwa, bai shirya ba! Bai shirya tashin hankali a yanzu ba ba yanzu ba da yake jin son Afeefah yayi mishi yawa a zuciya. Da sauri ya juyo kan motar dama bai yi nisa ba ya dawo wani irin parking yayi ya sauƙa ya nufi sashen Boys quaters ɗin yana Adu'ar Allah ya sa kar mommy tayi mata wani abu, sai kace- nace ya same su suke yi ana ta maida magana, Afeefar na tsugune kaman mai neman gafara tana kuka. Gaban mommyn ya je kusa da Afeefar shima ya duƙa kawai ba tare da ya furta kalma ko guda ba. "Saleem" Ta ƙira sunanshi ya amsa ba tare da ya kalleta ba "Ɗago saleem ka kalleni, ka ɗago ka tabbatar min da kai ke tura duk wani saƙo da na gani wayar yarinyar nan, da gaske kai ne kake son wannan marar cikakken asalin?" Ya runtse ido wani irin nauyin Afeefah yake ji kaman yayi yaya, baya so baya kaunar ta ke jin furucin ɓatanci daga ahalinshi zuwa gareta musamman mahaifiyarshi. "Mommy ni ne, Son ta nake kuma aurenta nake Son y...." Wani irin mari ta ɗauke shi da shi, karo na farko kenan da ta kai hannunta jikinshi don shi yaro ne mai tsananin biyayya a gareta. "Maimaita!" Ta daka mishi tsawa ya sake cewa "Mommy ina ƙaunarta, kuma aurenta nake buri" Wani marin ta sake dauke shi da shi, ba shi kaɗai ba har su sadiqa sun tsorata basu taɓa tunanin za ta iya kai hannunta jikinsu ba don ita Allah yayi ta da tsananin son yaranta, hawaye take yi ta sake cewa saleem ya maimaita "Mommy... Mommy da gaske zuciyata ta kamu da Soyayyar Afeefah da ba na tunanin ko wani hukunci za'a yi min zai sa ta fita daga ciki, mommy kila sai kin cire zuciyar gabaɗaya daga kirjina za ki daina jin harshena na furta kalmar ƙauna zuwa gareta..." Wani irin kuka Sameerah ta fashe da shi, a yanzu ta yarda ta yarda ba wani asiri don tabbas abin da take ji a kan Sulaiman shi ke azabtar da Saleem tunda har zai iya mayarwa mommy magana sau uku, Mommy ta sake ɗaga hannu zata mareshi sadiqa ta riƙe hannun tana hawaye "Mommy ba shi za ki daka ba ga Mayyar da ya kamata ki kassara chan, wallahi Afeefah sai kin bar gidan nan ba za ki tarwatsa mana gida ba" Afeefah dai ta rasa yanayin da take ciki, wani irin ƙauna da tausayin saleem ne suka sake mamaye zuciyarta ko tunanin inda za ta nufa in sun kore ta bata yi, damuwarta saleem idan suka raba su basu mishi adalci ba, shi ya cancanci bautar ta na aure har mutuwa. "Saleem!" Mommy ta kira shi karo na ba adadi muryarta har yanzu da wani irin mamaki, idanunshi da suka sauya ainun ya ɗago ya kalleta tamkar ba soja ba wani irin rauni ya bayyana karara a fuska da idanun nashi. "Saleem!!" Ya amsa a hankali "Saleem!! Sau nawa na kira ka?" A hankali yace "Uku" "Wannan ba aikin hankali bane na asiri ne, amma ko da asirin ai ka san matsayi na a wurin ka ko? Ka san ni wacece ko?" "Mommy ke mahaifiyata ce kina da darajar da babu wanda yake dashi a wurina duk faɗin duniyar nan. Kin isa da ni kuma na san za ki so farin cikina! Mommy a yanzu ba na jin ina da wani buri da zai haifar min da farin ciki kaman Afeefah, ban san sadda sonta yayi min wannan kamu ba don ba ya shawara kan ya shiga wallahi ina sonta! Ba zan iya rarrashin zuciyata ba don so bai san rarrashi ba..." "Afeefah Allah ya isa tsakanina da ke! Allah ya isa" Mommy ta faɗa tana kuka. A lokacin hawayen da saleem ke danne wa suka gangaro ya ɗago ya kalli mommyn zai yi magana ta daka mishi tsawa a kan ya mata shiru "Aure kake so zan ɗaura maka aure da yar ɗan uwana Sabreena da take sonka tun bata san kanta ba, amma soyayya, magana ko zancen aure tsakaninka da wannan yarinya saleem har Abada, ko bayan raina ne Allah ya isa ban yafe ba! Wallahi wallahi sai na iya tsine maka ka sake shiga huldar yarinyar nan ko a hanya kuka haɗu ban yafe ba ka mata ko da sannu ne... In har ni na haif...haifeka Saleem sai dai in kana da wata uwar za ka iya" A razane yake kallonta, ta share fuskanta ta dubi Samha "Je ɗakina ki ɗaukomin akwatin da ya fi kowanne girma" Da sauri ta tafi, Sameera zuciyarta ne ke tsitsinkewa a yanzu tsoro ne ya rufeta, wlh tana iya jin irin abin da saleem da idanunshi ke runtse yake ji a yanzu, gabaɗaya jijiyoyin kanshi sun mimmiƙe girgiza kai take yi "Mommy don Allah ki dakata! Ki tsaya kar azabar yayi mana yawa... Ki barta don Allah ko bai aureta ba ta z..." Sadiqa ce ta kai mata duka "Kema asirce ki tayi don ƙaniyarki? Wallahi ta gama zaman gidan nan" A lokacin Samha ta shigo da wani cream trolley. Mommy ta karɓa ta jefa mata "Na tsani ganin ko inuwar ta ne, ku gaya mata ta tattari duk taeukucenta ba na son ganin ko ƙyallenta a gidan nan kar ma ta dawo cikin dare ta kama wani biya... Har Abada ko magana ta yi wa dana sai na tabbatar ta kare rayuwarta a gidan yari" Ko gwada roƙon su bata yi ba don ta san ko sama zai haɗu da kasa a yanzu mommy ba zata amince da hakurin ta ba, kuka mai sauti take yi jikin saleem ne ya fara rawa, ba zai cigaba da sauraron kukanta ba ba zai iya ganin tafiyar ta ba, zuciyarshi tamkar zai fashe saboda tsoro da fargaba in ta fita ina za ta je? Wa ta sani a duk faɗin Kaduna? A hankali ya miƙe jiri na kwasar shi a dafe da gini ya cigaba da tafiya har ya bar ɗakin zuwa lokacin da gaske yake hawaye, hukuncin Mommy tamkar zare mishi farin ciki tayi a wannan rayuwa, tamkar ta kulle shi ne a magarƙamar da ya fi kowani magarƙama duhu da azaba. Afeefah ta haɗa komai nata, wayar da saleem ya saya mata kawai ne ke riƙe hannun mommy kan suka tasa ta gaba har wajen gate, ta jima tsugune a wurin tana kuka kan ta miƙe ta share fuskarta ta ja akwatin ta fara tafiya. "Hasbunallahu wani'imal wakeel...! Innalillahi wainna ilaihi rajiun" Abin da take ta nanatawa kenan tana share hawaye ta yi tafiyan da bata san adadi ba har ta fito wani babban hanya dake dauke da ababen hawa fiye da cikin unguwar da ta bari, nan ma miƙawa kawai tayi ta cigaba da tafiya ko biyar babu a hannunta, ta fi awa biyu tana tafiya janye da trolley ɗin lokaci lokaci ta kan share hawaye masu zafi dake zuba mata, a daidai wani wurin ba da hannu ta tsaya ta ɗaga kai ta kalli garin, mutane ne ke ta hada hada kowa harkar gabanshi yake yi, daidai wutan ya nuna ja motoci suka tsatsaya wani daga gaba yayi kokarin kin bin doka sai hatsari ya faru a wurin tuni go slow ya wani irin haɗuwa. Tana tsaye har lokacin rike da akwatinta kamkam sam bata san me za ta yanke ba, bata san ya za tayi ba kaman an ce ta ɗaga kai sai idanunta da suka zama wasu iri tsabar kuka suka shige cikin nashi daidai yana sauƙe glass, kallon seconds biyar suka yi wa juna ya ɗauke kanshi ya mayar gaba yana tsaki, ita kam bata dauke kai ba sai take jin kaman ta je ta roƙe shi ya taimaka mata ko da ya haɗa ta da Sulaiman ne, amma kuma Sulaiman ai bai san wacece ita ba idan su ma suka kore ta fa? Innalillahi wainna ilaihi rajiun ta sake faɗa hawaye na silalo mata daidai ya sake kallonta idanunshi suka sauƙa kan hawayen a lokacin suka samu hanya ya ja motar ya bar wurin. Juyawa tayi ta cigaba da jan trolley ɗin dama ta sani bashi da kirkin saleem, babu mai kirkin saleem ma a duniyarta shi kaɗai ta sani mai kirki, daidai ta zo gaban galaxy mall da ta gani rubuce sama za ta wuce sai tayi karo da wata mata, baya baya matar tayi za ta faɗi Afeefar tayi hanzarin sake akwatin ta riƙe ta "Subhallah! Ki yi haƙuri" Ta faɗa cikin dasasshiyar muryarta, sai ta ga matar ta kasa tsayuwa numfashinta na ta kai komo ga ta dai cikin shiga na alfarma har da jaka a hannunta "Lafiya Aunty? Ko baki da lafiya ne?" Take ta tambayar cike da damuwa matar ta kasa magana. Hankalin Afeefah ya tashi, kar ta mutu yanzu ma a ce ita, ya zata yi? Ba Za Ta iya barin ta a nan ba a haka yadda take duk ta fice hayyacinta ta jike jagwaf da gumi Dukda sanyi ake. Wani tunani ne ya faɗo wa Afeefah ta yi hanzarin karbar jakar matar tana cewa "Aunty taimakon ki zan yi ba sata zan miki ba bani da ko biyar da ba zan taɓa jakanki ba" Buɗewa tayi ta samu ɗari biyar bata tsaya tunani ba ta tari abin hawa ta sanya matar a ciki itama ta shiga mai machine ɗin ne ya dauka mata akwatinta tana ce mishi "Asibitin dake kusa don Allah" "Sannu, Sannu" Take ta maimaitawa matar gwanin tausayi sai taji tana yi wa Allah godiya da ya barta da lafiyanta ko ba komai ta tsira da shi, a haka suka isa wani private hospital ya shiga da su har ciki aka dauƙeta emergency zuwa lokacin bata numfashi. 🖤Gureenjoh🖤 HAIHUWA DA HANJI (A True life story) Fatima Muhammad Gurin (Gureenjoh) Wattpad-Gureenjo6763 Arewabooks-Gureenjoh *FREE BOOK* *018* Sai da ya bar gida da motar ya fahimci gas din Ac ɗin shi ya ƙare, hakan ya ɓata mishi rai don baya son buɗe glass na mota yana tuƙi, a haka ya tafi Asibiti yayi abin da zai yi a ranar wuraren sha biyu ya bar asibitin ya nufi gida, a daidai babban titin da zai ɗauki hanyar cikin unguwar su na Barnawa hold up ya riƙe shi, a dole ya sauƙe glass saboda zafin da yake ji. Karon farko da idanunshi suka sauƙa a kanta bai gane ta ba sai da ya ɗan yi focusing na seconds kan ya gane ta, wannan yarinya ce da ya taɓa ceta from poison, wannan yarinya da saleem ke so, sam bai yi tunanin wani abu ne ya tsayar da ita a wurin ba sai a karo na biyu da ya mayar da idanunshi wurin suka sauƙa a kan trolley dake gabanta, idanunta ya sake mayar da ido sai ya fahimci ta yi kuka sossai, horn ake ta danna mishi hakan ya sa ya ja motar yayi gaba wayanshi ya zaro ya shiga neman Layin salim sai dai har 2missed calls ya mishi bai ɗaga ba shi da ya tsani kira sau biyu ya kan ce ai duk uzurin da mutum ke yi in ya zo ya ga na farko zai bi ba sai ka ta jera kira kaman marar aikin yi ba, a kira na uku saleem ya ɗaga sai dai ya kasa magana. "Saleem are you Okay? Whats wrong with ur voice?" Saleem ya kasa magana don shi kaɗai ya san me yake ji, Ryan bai taɓa jin Muryar abokin nashi a haka ba, dole ya nemi wuri yayi parking "Saleem Mommy ce?" Yayi uttering "Uhmm Ryan Mommy ta kori Afeefah ban san wani irin hali za ta faɗa ba, mommy tayi alkawarin tsine min na sake ko da magana da Afeefah ne bare yunkurin taimako aure ko soyayya, she's too young Ryan she's too young! Na san tana chan all alone, scared and disturbed idan wani abu ya same ta fa? Its all my fault da na fara son ta Its my fault..." Hawayen da yake yi ne ya sa ya datse lips ɗin shi da ƙarfi sai kawai ya katse wayan. Kunna motar rayann yayi yana jin wani abu a ƙasan ranshi, tausayin Saleem ya rufe shi haɗe da damuwan jin halin da yake ciki bai taɓa jin abokin shin haka ba, saleem da ko haɗe rai baya yi. Fuskarta yake gani a idanunshi ashe kallon taimako take mishi, steering ya ɗan buga da tafin hannunshi yana zagayowa inda ya barta sai dai neman duniya bai ganta ba, har parking yayi ya sauƙa yana takawa da kafa ya zazzaga bata nan. Bakinshi ya ɗan taɓe kaɗan yana shirin juyawa wayanshi yayi ringing. Zarowa yayi sai ya ga Driver ɗin Mamminshi ne, dagawa yayi "Ado ya aka yi?" Ya fitar da maganan yana lumshe ido sam ba zaka san yana da damuwa ba ko hankalinshi ya ɗan tashi don fuskar bai nuna ba ko da wasa. "Oga akwai matsala ne, Hajiya ce!" Tuni ya ware idanun a take suka sauya ya fara nufar motanshi yana ji Ado na mishi bayani wai ya kaita sayayya kuma yayi ta jira bata fito ba ya shiga ciki kuma yayi neman duniya bai sameta ba. "A ina ne?" "Galaxy mall" Yana kusa da wurin ƙarasa wa kawai yayi "Ka ƙirata?" Ya jefawa Ado tambayar Ado yayi saurin duƙar da kanshi don ya san fushin Rayyan a take sai ya haukace, idanunshi sun yi mishi kwarjinin da ba zai iya kallon cikinsu ba "Ban fito da waya ba" Wani irin kallo ya watsa mishi lip ɗin shi ma sun yi nauyin buduwa bare su sake furta ko da kalmar A. Wayanshi kawai yake dannawa ya shiga ƙiran layinta sai dai ringing na duniya ba'a ɗaga ba, tracker ya shiga na Find my Iphone tuni ya ga location da take, a maimakon hankalinshi ya kwanta sai hankalinshi ya sake tashi ba za ka sani ba amma in ka ƙura mishi ido zaka ga hannayenshi har rawa suke idan kuma ka taɓa za ka ji sun yi sanyi tamkar ƙanƙara to baya cikin lafiya kenan. Mota kawai ya shiga ya ja tafiyar mintuna goma ya isar da shi asibitin yayi rough parking ya sauƙa ya nufi ciki, a gaban nurses station ya tsaya "An kawo wata elderly woman yanzu! Where is she?" Da ɗan karfi yayi maganan don ya ga mace ɗaya ce kawai ta mayar da hankali kanshi tsawar da yayi ya sa duk suka juyo, kofan emergency kawai ta nuna mishi ya nufi wurin kawai ya tura ya shiga. "Excuse you! Baka san ba'a shiga nan bane?" Id card ɗin shi ya fitar ya nuna musu idanunshi na kan Mammi da suke ta ƙoƙari wurin ganin sun ceceta ya furta a hankali "The patient is experiencing end-stage renal disease(ESRD) nd she's diabetic i hope ba ku yi kuskuren komai a kanta ba" Ja da baya wanda ke rike da drip yayi don ba ruwan masu sugar bane, Id card ɗinshi kuma ya tabbatar musu da waye shi. A tare da shi aka cigaba da ƙoƙarin ceton Mammin kusan awa ɗaya da wani abu kan suka fara fitowa aka barshi shi kaɗai. A kan kujera ya zauna ya sa hannu ya riƙe nata ɗaya ya gimtse a duka hannunshi biyu ya ɗora goshinshi a kai yana jin jininshi na cigaba da tsitstsinkewa rauni mai girma ne da ba zaka ɗauka irin shi mai dakakkiyar zuciya zai nuna ba bayyane a fuskar shi da ma idanunshi, ƙiran sallah ne ya sa ya ɗago a hankali ya zuba mata idanu sama da mintuna uku kan ya mayar da hannun a hankali ya ajiye mata ya miƙe ya fito Fuskarnan babu ɗigon walwala, a kan trolley idanunshi suka fara sauƙa ya ɗan kalli Ado da ke maƙure gefe kaɗan kaman zai yi magana kuma sai ya fasa yayi gaba, sallah yaje yayi bayan ya idar ya dawo yana shigowa reception ɗin tana ɗagowa suka haɗa idanu, handbag ɗin hannunta ya ɗan kalla kan ya nufeta. Yana matsowa dukar zuciyarta na ƙaruwa gabanta sai dukan uku uku yake tamkar za ta rasa numfashinta take ji don bai daina kallonta ba kuma bai daina nufarta ba kamshinshi ya riga shi isa, ko kan ya iso aka ƙira shi "Sir the patient, ta farka" Numfashi kaɗan ya sauƙe ya juya ya nufi ɗakin, bata san ta kama numfashi ba sai da ya ɓace mata taji tana kokarin mutuwa ta sake shi da ƙarfi tana dafe kirjinta, Allah ya gani tsoron shi take bata sani ba ko tun ihun da yayi mata ne tayi developing wannan tsoro ko yaya amma muddin ya sauƙe ido a kanta sai ta ji wani tension na building inside her. Idanu kawai ya zuba mata ta ɗago ido ta kalleshi cikin ƙarfin hali ta sakar mishi murmushi tare da miƙa mishi hannunta, ya taka a hankali yaje ya kama yana zama "Mammi..." Sai yayi shiru ta sake yin murmushi mai kyau "Saraki na ji sauƙi ka kwantar da hankalinka, sannan am sorry na ji ina son ɗan shan iska ne ya sa na fita not knowing hakan zai faru am sorry na ɗaga maka hankali" "Mimmi stop it please, am sorry i wasn't there to take you out myself da kin faɗa min zan bar duk abin da nake zan zo na kai ki na kula da ke har mu koma, Its my fault da nake emphasizing akan zaman gidan am sorry you get bored" Hannunshi ta ɗan matse tana murmushi har lokacin, ɗago ta yayi ya buɗe ruwa ya bata ta karɓa babu musu ta sha sossai kuwa don masu ciwon su na buƙatar enough ruwa a jiki. Basu wani jima ba suka fito yana riƙe da ita, har lokacin in har ka san shi sosai za ka hangi akwai damuwa a fuskar shi, Afeefah da har lokacin tana zaune a wurin tayi saurin Miƙewa ganin su tare, dama ya san matar? Menene alaƙarsu? Ta ya aka yi ya san tana nan? Su ne tambayar da ta tsaya yi tana daga tsaye tana kallon su. Idanun Mammi ne ya kai kanta, sai ta dakata tana tunani ga jakanta dai hannun stranger a hankali take tuna abin da ya faru yarinyar ce ta taimaketa, ta yi mamaki ƙwarai ganin yarinyar har lokacin kuma riƙe da jakanta da alama ko ajiye shi bata yi ba, tana tuna kalaman yarinyar na ban haƙuri a sadda ta ɗauki ɗari biyar ciki. "Saraki wanchan yarinyar ita ta taimakeni ta kawo ni nan, da ban san me zai faru ba" Kaman bai fahimta ba ya sake kallon Afeefah, chan ƙasan ranshi ya ji daaɗi kuma ta samu wani ƙima a idanunshi saboda duk wadda ya kaunaci Mammi ko da bai kaunaceshi ba shi ya bashi daraja na musamman, sai dai har lokacin fuskar shi bai nuna ba sai nufanta da Mammin ta sa suka yi, ita abin da ya kaɗa ta ma tahowarsu tare, ita dai ta rasa wannan irin razani da take shiga da kwarjinin wannan bawan Allahn, ko da suka tsaya gabanta sai ta ga ya cike wurin gabaɗaya, kuma kallonta yake don Mammi ta sake shi ta kama hannunta. "Ɗiyata yaya Sunanki?" "Sunana Afeefah, Aunty ya jikin ina fata komai lafiya?" Tayi maganan kaman mai tsoron wani abu zai kama ta "Alhamdulillah Afeefah, na gode ƙwarai da kyakyawar tunanin ki ba kowa ne zai iya irin taimakon da kika yi min ba, Allah ya saka da alkhairi" Afeefah tayi murmushi "Babu komai Aunty, ga jakarki ki yi haƙuri na cire ɗari biyar a ciki mun hau adaidaita saboda ba ni da ko biyar" Murmushi Mammi ta saki ta ɗan kalli Rayyan da bai ce komai ba ya zuwa yanzu ya kawar da kai daga kallonta sai dai yana sauraren su. "Gaskiya samun irin ki a wannan zamani sai an tona" Idan ta tafi da jakar nan ba karamin abu za ta samu ba don bata tantama har zobunan gwagwalanta suna ciki amma bata ko buɗe ba bare tayi tunanin yi mata sata, hakan ya matuƙar burgeta. "Saraki mu kai ta gida ko? Ina so in ga gidansu in yi ma iyayenta godiya kuma in basu hakurin rashin ganinta kan lokaci" Ta kalleshi shima ita ya kalla bakinshi ne yayi mishi nauyi, kuma ba ya son dogon bayani sai ya kalli Afeefar da kanta ke ƙasa kaman daga sama ta ji ya ce "Kina da gida?" Yayi maganan yana ɗage gira ɗaya. Mammi ta Harare shi "Wani irin tambaya ne wannan akwai wanda ya faɗo daga sama ne?" Ita dai tambayar ya zo mata wani iri sai hawaye suka cika idanunta a lokacin ta tuna ashe bata da inda za ta je, da alamu kuma ya sani don maganar shin ya fi yi mata yanayi da gatse, a hankali ta kalli Mammi "ba sai kun kaini gida ba Aunty, kina bukatar hutu saboda jikinki daga nan zan koma da kaina" Tayi saurin juyawa amma duk da haka ya ga hawayen da ya silalo mata, Ado ya kalla "Ɗauki akwatin nan mu tafi" Yana kai nan ya fara kokarin kama mammin "She has No where to go, for now za mu tafi tare" Cike da tausayi Mammi take kallonta, so take ta ji karin bayani me ya sa bata da inda zata je? Ina dangin ta in bata da iyaye? Amma sanin duk ba yanzu bane lokacin maganar ta saki Rayyan ta riƙo hannun Afeefar galala yayi yana kallonta ko ta tsaya don ta san rigimar shi, haɗe fuska yayi sossai ya biyo bayansu. Sanin halinshi ya sa Mammi ta zauna gaba Afeefah ta shiga baya, ya ja motar a hankali ya fita daga asibitin, Ado ma ya bi bayanshi har yanzu zuciyarshi bai dawo daidai ba yana tantamar ko Rayyan ya barshi ko sai ya ɗauki mataki a kanshi don abin da duk ya shafi Mammi baya wasa da shi sam kaman yadda ita ma bata da kaman Rayyan a duniyarta. Shiru motar yayi don Mammin na buƙatar hutu so ganin ma kaman ta gaji da zaman ya nemi wuri yayi parking, ya ɗan koma baya ta yadda ya sake birkita Afeefah dake zaune saitin kujeran shi ya sa hannu ya kwantar da seat ɗin mammin a hankali, ta buɗe ido ta kalleshi ta ɗan yi murmushi kawai ta sake lumshe ido ya furta "Sannu" Cikin tsantsar kulawa, sai kallonsu Afeefah take yi. A iya zaman nan ta fahimci matar tana da matuƙar muhimmanci a rayuwarshi Dukda bata ga kama ba don matar baƙa ce kaman ita shi kuwa farin shi har ya ɓaci, ba zaka taɓa cewa bai hada dangi da Larabawa ba barin ma kasumba da gemun da ya ajiye ɗan daidai da shi baƙi sidik. Motsin kirki bata iya yi kamshin motar har yana hawa mata kai a haka suka isa wani tsararren unguwa shiru ne unguwar kaman ba titin da suka baro ke ɗauke da hayaniya da jama'a ba, nan ɗin gidajen manya manya ne, sai dai ka hangi su dawisu da su jimina a gidajen da gininsu ma na zamani ne, gaban ko wani gida kuma akwai securities zaune kusan kowanne sanye da uniform ko yellow ko blue, a hankali ya gangara gaban wani golden gate mai girma fuskar sai sheki take horn yayi, sai gashi an leƙo wannan ɗin ma na sanye da blue riga da bakin wando, Gaisuwa ya shiga miƙawa Ogan nasu ya ɗaga mishi hannu kawai don Window na sauƙe saboda rashin Ac. Tamfatsetsen gida ne don yayi na su Saleem sau uku ko biyu da rabi, gidan tamkar ginin sarauta saboda fari ne kal an mishi ado da golden paint har kwanon golden Color ne, harabar na shimfide da interlocks ɗauke da shukoki masu tsananin kyau da ɗaukar ido, Dukda akwai parking lots har uku jere da motocin alfarma bai yi parking a ciki ba sai da ya je dab kofar shiga yayi parking ya sauƙa ya zagaya ya buɗewa Mammin kofa. Ita dai Afeefah na ta mamaki don bata zata akwai wanda wannan mai zafin ran ya dauka da muhimmanci ba haka, bata taɓa zaton zai iya buɗewa wata macen kofa ba kila dai mahaifiyarshi ce, kila kuma kamannin mahaifinshi yayi shiyasa basa kama ko ta wani ɓangare. "Afeefah sauƙo mana kin zauna ciki" Ta faɗa a hankali, buɗe murfin tayi ta sauƙa tana jin kanta dake sara mata na ƙaruwa saboda tsabar kukan da tayi yau, kunyar hijabin jikinta take don onion colour ne kuma duk gaban da ya jike da hawaye ya bushe sai yayi wani jirwaye jirwaye, A baya ta bi su har suka shiga cikin tsararren parlorn mai girman gaske sanyi ne ke ratsa ko ina ga kamshi, parlorn kal kal kaman a zuba maka abinci a ƙasa ka ci komai na parlorn royals ne golden and milk, tana kuranta kyaun gidan su saleem wannan gida ya fi nasu tsaruwa nesa ba kusa ba. A cikin kujera suka samu wata budurwa ganin Mammi ya sa ta tashi da gudu ta nufeta sai dai hararar da Ryan ya sakar mata ya sa ta fasa isa da gudun ta ɗan natsu "Mammi are you Okay? Me ya same ki? Na dawo daga school wai kin fita Mammi jikinki yayi kyaun da za ki fita? M..." "Will you shut up and let her rest?" Ya faɗa ba da tsawa ba sai dai ba kuma da wasa ba, mammi ta ɗan yi murmushi "Abeeha ga Afeefah ki kai ta ɗaki na musamman a kai mata abinci tayi wanka ta kwanta ta huta sossai please she's exhausted daga alamunta" Kallon Afeefah Abeeha tayi sai ta juyo zata fara jero wa Mammi tambayoyin ina ta samo ta sai suka haɗa ido da Ryan tuni ta wuce ta kama akwatin da Ado ya shigo da shi suka yi wani ɓangaren daga cikin parlorn. A hankali suka isa wani matakala uku suka hau zuwa wani corridor da ya ji interior kan suka shiga wani parlor madaidaici kuma tsararre grey ne da Black colour, bai barta nan ba sai da ya sadata da cikin bedroom ɗinta duk ko ina suka bi kalkal yake gidan kaman kullum ake wankewa, a bakin gadon da shima Grey ya ji shimfida White ya ajiye ta ya buɗe wani frigde dake gefe ya fiddo ruwa marar sanyi sossai ya bata ta sha sossai kan ta ɗan kwanta "Sannu Saraki Allah yayi maka albarka" Idanu ya lumshe ya buɗe tuni suka ɗan sauya, a hankali ya amsa da Ameen kan ta ɗan kwanta tana sauƙe numfashi. "Mammi ki huta sossai please, bana so in tafi in barki amma Saleem bashi da lafiya i need to go and see him, ba zan jima ba zan dawo" Tayi murmushi "Su fa Maryama suna nan kar ka damu take your time, kuma ma Abeeha ba ta dawo ba na san tana gamawa da Afeefah zata zo" "Ta ishe ki da surutu dai" Yana kai nan ya miƙe tana mishi sai ya dawo ya gaishe mata da saleem ya fice. Wani motar daban ya ɗauka mai Ac ya fice daga gidan bayan ya umurci Ado da ya fita da wanda ya dawo ya kai a saka Gas na Ac, kai tsaye gidan su Saleem ya nausa bayan ya isa ya bi ta baya ya haye saman zuwa ɗakin saleem ɗin komai a kashe ya samu kaman ba mutum, hasken ya kunna ya nufi cikin ɗakin sai ya samu saleem lullube da bargo, kanshi ya nufa ya janye bargon ya sa hannu a goshinshi ya janye "Subhallah! Saleem you are burning up tashi mu tafi hospital" "Ryan Afeefah, ban san wani irin hali zata faɗa ba am scared kar Allah ya kama ni da laifi... Please help me find her please" Da kyar yake maganan saboda zazzafar zazzabi dake kassara gaɓoɓinshi. "Za mu same ta, In shaa Allah i will find her lafiyarka First ur temperature is very high" 🖤Gureenjoh🖤 HAIHUWA DA HANJI (A True life story) Fatima Muhammad Gurin (Gureenjoh) Wattpad-Gureenjo6763 Arewabooks-Gureenjoh *FREE BOOK* *Ku min uzuri da rashin amsa comments please matsalar wayata ta saka sai na nemi wani wayan nayi connecting hotspots saboda gidan sim din ta ƙi gyaruwa, please bear with me idan na tara comments ina bi in karanta na gode sossai da sossai. Anjima zan samu in duba idan na ga an zuba yadda ya kamata in shaa Allah za ku ji ni da dare* *019* Ko sanar da mutanen gidan bai yi ba suka tafi asibiti kai tsaye Amenity ya sa aka kai shi ya fara bashi taimako saboda abin ya Buge shi sossai, tausayin Saleem ɗin ne ya rufe shi mahaifiyarshi bata yi mishi adalci ba amma uwa ce ya suka iya? A chan gida kuwa Mudi ne ya shiga ya same su duk suna zaune a parlor fuskokin su babu walwala. "Hajiya Oga saleem ne..." Da sauri Sameera ta katse shi "Yayi me?" "Babu lafiya yanzu Oga Rayyan ya fita dashi jikin dai babu daaɗi ban gan ku ba nake tunanin baku sani bane" Samha ta ce "Mun shiga uku, duk akan Afeefar ne?" Shi dai mudi shiru yayi karshe ma ya bar parlorn, Sameera ta ɗauki mayafi tana kallon mommy dake zaune har lokacin, sadiqa da Samha ma suka miƙe Sameera tace "Mommy ki tashi don Allah mu je muga ya jikin nashi, mommy kaman ba a yi mishi adalci ba wallahi..." "Ba zan je ba ki ja ni ki kai ni, babu inda zan je ya gama ciwon ya dawo ya same ni, ba dai a kan wanchan Mayyar ba ce? Zai yi ya gama Rabuwa kam sun rabu na har Abada" "Amma mommy ya kamata dai ki je ciwo ai ya kore komai" Sadiqa ta faɗa, Samha tayi fuskar tausayi bata san haka abin zai kasance ba da bata janyo wannan rigimar from First place ba, suna son dan uwansu basa son ganinshi cikin wani hali. Duk yadda suka yi da mommy akan ta je ta ƙi haka suka tafi su uku, suna ficewa ta sabi gyale itama ta dauki mota ta bar gidan. Tafiya mai nisa tayi kan ta iso inda ta nufa, wani gida ne tayi parking gidan dai daga gani Talaka ne mamallakinshi don ya tsufe har ya gaji, ta sauka ta shiga ciki da sallama. "Ah Hajiya Hussaina ce tafe? Maraba sannu da zuwa sannu da zuwa" Matar da daga ka ganta ka san suna cikin wahala daidai gwargwado ta faɗa tana ɗauko taburma sabuwa ta shiga shimfida mata zama tayi suka shiga gaisawa, bayan sun gama tana ɗan kallon cikin gidan tace "Yaya fa? Allah ya sa dai bai yi nisa ba" Tace "Yanzu kuwa ya fita amma babu jimawa zai dawo don abu ya je karɓo wa nan kusa da mu" "Ina yaran? Ina sabreena?" "Duk fa sun tafi Allo, ita sabreena suna bukin ƙawarta ta fita" Bata gama magana ba kuwa sai ga Yayan ya shigo. "Hajajju ke ce a gidan maraba sannu da zuwa" Gaisawa suka yi Dukda yayanta ne sai dai shi ke bata respect duk saboda kuɗi masu gidan rana. "Ina soja marmari daga nesa? Sati biyu kuwa da ya shige ya aiko mana da kayan abinci wane Allah dai yayiwa rayuwa Albarka ya cigaba da buda mishi" "Ameen yaya, dama maganan da ta kawo ni kenan ma akan shi... Ka san akwai batu a kanshi da sabreena da take ta mutuwar sonshi shi kuma yana nuna baya so, to yanzu zancen da nake maka wata yaje ya ɗauko chan wani kauye ta asirce shi tun kan ma ayi auren sai maganarta yake ji yanzu haka saboda na raba su yana chan kwance gadon asibiti" Gaje da Yaya suka hada baki suka ce "Eyeee ka ji min yaran zamani ki samu mutum da uwar shi ki so raba su? Amma Saleem dai yayi ragon azanci ina shi ina irin waennan matan?" "Shiyasa nake so a tado magananshi da sabreena da na ɗauka wata mai hankali zai ɗauko mana ashe dai shima hankalin bata ishe shi ba, na kuma ga gida bai koshi ba ai ba za'a kai waje ba, idan ba damuwa ma bana son auren nan ya ɗauki lokaci ko wata bana so ya rufa ta zo tayi jinyarshi" Gaje ta washe baki, Yaya dai ya ɗan yi shiru kan yace "Toh ai wani hanzari ba gudu ba, kin san bamu ajiye komai ba na shirin aurar da sabreena" "Yaya duk wannan ba komai bane, ni ce nan uwarta ni ce ubanta ita kaɗai nake so" "Toh ai shikenan Allah ya shige mana gaba" Suna cikin maganan sai gata ta shigo sanye da hijabi har ƙasa ganin mommy ta tsuguna "Sannu da zuwa mommy" "Sabreena ba zan amsa ba, yaushe rabon ki da gidan mu? Tun su Samha na jaje har suka gaji" Baki ta ɗan taɓe tana ayyana su kuma dayake basu san inda nake ba ba, ai ina sane da kyamar gidan mu suke ji shiyasa basa zuwa. "Mommy islamiyya ne duk ya riƙe ni kin san muna ta shirin sauƙa" "haka ake so ai Allah ya taimaka" Daga nan bata wani jima ba tace zata tafi suka raka ta har mota kan suka juyo gida. Wani irin guɗa gaje ta saki "Malam!!! Kukanmu ya kusa yankewa nesa ta matso kusa" Shi dai wani kalar murmushi yake, Sabreena ta cire hijabin jikinta ta jefar Sanye take da wata fitted gown na lace da aka yi wa arniyar ɗinki da ya bayyana komai nata, kanta attach ne da ya zo har duwawu ta ja tsaki. "Ke 'yar gari ya aka yi kika ankare tana nan?" Gaje ta faɗa tana kai mata duka kamar kawarta "Motar ta na gani nayi maza na shiga makota na ari hijabi na wanke fuska na cire eyelashes da nails ɗina gashi a banza bata bani ko biyar ba mata sai makon bala'i" "maganar aurenki ya kawo ta, nima zan so a zo ayi saboda na gaji da gani gani da ake yi min a unguwar nan, ita kuma Hussaina a zaton ta banza ya faɗi ne zata ɗauka bata san ta daukawa kanta wuta ba... Ai yadda uwata bata taɓa kaunar nata uwar ba nima ban taɓa ƙaunarta ba kuma ita ma haka da tana ƙaunata da bata barni nan cikin wahalar talauci ba" Haka suka dinga tattauna yadda za su ci arziki don mommy ta jima da tsaya musu a wuya kaman kashin kifi, don ma saleem mutumin kirki ne mai son zumunci baya wata bai turo musu wani abu ba amma ita kam bata tunawa da su sai in bukatarta ne ya tashi, ta watsar da dangin tamkar kashi an ɗauki Ƙawaye masu kuɗi an manna a jiki har kunyar nuna su take. Sabreena dai da farko yarinya ce natsatsiya amma zamani ya zo mana da wani abu, iyaye ba ruwansu bane yaro ya tsaya yayi karatun islama ko kar yayi, damuwarsu dai a nema ko ta wace hanya, babu kwaba babu cikakkiyar tarbiya, tun tana dai yin abin saffa saffa yanzu babu wanda bai san Sabreena 'yar karya ba, barta da son karya yau wannan saurayi gobe wanchan don tana da kyau kuma suna kashe mata amma dai ita ta riga ta saka saleem ne mijinta tunda iyayenta suka kwadaita mata hakan a ganinsu duk samarin ta ba zata yi mai kudin saleem ba. Ita kuwa mommy tana shiga mota tayi murmushi "Gwara ka auri wacce ko kwanciya na ce tayi in bi ta kanta zata kwanta, wacce dole ku haɗu ku bi umarnina tare akan ka kwaso wacce zata raba ni da kai ko ta hanyar soyayyace kuwa bare uwa uba asiri" Daga haka ta ja motar ta bar unguwar tana kwafa. **** Afeefah kam suna shiga ɗakin da Abeeha ta kaita ta tsaya tana karewa ɗakin kallo, ɗakin yayi kyau kwarai kuma full furnished don kayan ɗakin milk da gold a gyare yake kaman akwai mutum ciki alhalin ba mai zama ɗakin tunda mai dakin tayi aure. "Feel free Afeefah ki yi wanka bari na sa a kawo miki abinci, in kin ci sai ki hau gado ki huta ko?" Ta kalleta sai taga murmushi take mata saɓanin ranar da ta fara haɗuwa da Samha ta tuna har wanke bayi Samha tayi da sunan tana kyamarta don kawai ta shiga tayi alwala, murmushi ta mayar mata tace "Na gode" "Mind not" Ta faɗa tana ficewa, a ƙasa Afeefah ta zauna tana dafe kanta da kaman zai faɗi, ta fara tunanin halin da Saleem ke ciki sai dai kuma tayi tunanin ba zai damu sossai ba idan Ryan ya faɗa mishi tana gidan su, jiri sossai yake damunta a haka ta lallaɓa ta miƙe ta shige bayin, wanka tayi tana raya a komai ma fa gaba da gabanta tana tunanin abubuwan bayi da ƙawa na gidansu saleem ne ƙarshe bata san akwai irin wannan ba, sai kuma ta fara tunanin kila suma akwai wanda ya fi nasu shiyasa Allah ma da ya tashi bai yi yatsun hannu daidai ba kowa da matsayinshi. Amma me yasa kirkin waennan ya bambanta da waenchan Dukda waennan sun fi su dukiya? Bata da amsar wannan tambaya ta wani ɓangaren kuma tana da shi don uwa nagartaccciya da suke dashi ya gama amsa mata komai, dafe da gini ta fito riga kawai ta saka ko abincin da aka kawo mata ta fito ta samu shirye a babban tray bata iya ta bi ta kai ba ta hau gadon ta dukunkune, zazzabi ne ya saukar mata ciwon kai da jiri kuma suke contributing. Kusan awa biyu tana cikin wannan yanayi tana ta hawaye, hawayen tunanin saleem bata san itama tana jin wani abu a kanshi ba sai da suka rabu, ko babu komai shine mutum na farko da ya bata dukkan kulawa da lokacin shi, ya nuna mata itama mutum ce kamar kowa, tana kukan maraici da tsananin kewan iyaye saboda shi ne sila tun farko. Knocking aka yi mata sai aka turo kofar da sallama aka shigo Abeeha ce "Afeefah" Ta ƙira sunan tana zagayawa ta kanta, ganin halin da take ciki ya bata tsoro "Subhallah! Baki da lafiya ne? Sannu bari na faɗawa Mammi ta kira Ya Rayyan ya zo ya duba ki" Bata jira amsar Afeefah ba ta fice da sauri. Ɗakin Mammi tayi ta shiga da sallama ta samu mammin ta idar da la'asar tana zaune ne kawai tana lazimi a hankali. "Mammi Ya Rayyan bai dawo ba? Ko za ki kira mana shi?" "Me ya faru? Ke fa kin iya rudewa a karamin abu" "Mammi wannan yarinya da kuka dawo tare Afeefah kin ji jikinta? Kaman wuta sai kuka take yi tana bukatar a duba ta ko mu tafi hospital?" "Subhallah! Tashi mu je in ga jikin" Har sun miƙe Mammi tace "Taho min da wayata" Taje ta ɗauka a bedside suka fita, a ta babban parlorn nan suka yi sashen da take ɗin wanda na 'yan matan biyu ne Jannah da tayi aure bai jima sossai ba sai Abeeha su suke rayuwa anan. Suna shiga Mammi ta hau gadon da taimakon Abeeha suka ɗaga Afeefar Mammi ta jinginata da kafaɗarta tana yi mata sannu cikin kulawa, wannan dumi na jikinta da kulawar sai ya sake karya zuciyar Afeefah tana tsoro! Tana tsananin tsoron su san tarihin ta suma su guje ta, tana son wannan dumi da kauna a tare da ita in ba haka ba kila mutuwa zata yi kawai sai ta fi hutawa, ta gaji haka zuciyarta ya fi glass tarwatsewa a yanzu haka. "Kira min Yayanku" Layin shi ta nemo a wayan mammin ta ƙira ringing na farko ya ɗaga da sallama. "Mammi jikin ne?" "No Saraki! Na ma ji ƙarfin jikin ka san abin kaman tashin aljannu yanzu sauƙi anjima babu sauƙi sai na Allah, ya jikin saleem ɗin?" Ya amsa cikin muryarshin nan "Ya ji sauƙi though he's still on admission, amma komai zai daidaita in shaa Allah" "Toh Allah ya bashi lafiya, ina so ka zo ka duba Afeefah fa ashe itama bata jin daaɗi jikin nan rau sai kuka take" Shiru yayi for seconds kan yace "Mammi bai wuci yunwa ba and stress she should just eat nd get enough sleep" "Ta ya mutum zai iya bacci with this temperature? Idan ba zaka zo ba in ɗauki mayafi in kaita asibiti" Zaune ya miƙe daga kishingiden da yake a office nashi yana wara ido, yaushe Mammi ta san yarinyar nan da har take mishi irin maganan nan a kanta? Yamutsa fuska yayi ko dai da gaske asirin take yiwa mutane da har ta asirce mishi Mamminshi? "Ina zuwa" Abin da ya fada kenan da kyar, Mammi ta kashe wayan Abeeha tace "Lallai Mammi kina so Ya Rayyan ya tsani yarinyar nan, tabbb he sound upset fa da yadda kika mishi maganarta yo ko mune bamu da lafiya ba sai ya gama shan kamshin shi yake duba mu ba, wani sa'in ba sai dai mu haƙura mu tafi asibiti ba ma" "Abeeha yarinyar nan haka kawai nake jin she gets special place in my heart, kin san taimakon da tayi min?" Nan Mammi ta shiga bata labarin abin da Afeefah tayi mata "Mammi wlh har Naji ina sonta sossai nima, to ina 'yan gidansu ina parents ɗinta?" "Ina ga sun yi magana da Saraki while i was unconcious don shi ya ce min bata da kowa" Afeefah dai na jinsu, tunda Mammi ta kira Rayyan tsoro ya rufeta, gashi ya ji haushin yadda mamanshi ta mishi magana a kanta kar ya zo ma yayi mata allurar da baƙar mugunta ita dai da an barta kawai. Suna ɗakin suna ta hira kadan kadan don Abeeha bata son zama baki shiru har Afeefah na mamaki kaman ba ƙanwar Rayyan da magana ke mishi wahala ba, ita ma dai bata ga kamanninsu ba sai dai Abeehar kyakyawa ce kuma ta fi Mimmi haske amma ba ta kai ko farcen Rayyan ba, bata gama nazarin ba ya shigo ɗakin hannunshi rike da karamar Red briefcase. Dammm haka gabanta ya buga, ya kalli Mammi da har lokacin Afeefah ke kan kafaɗarta ya wara kyawawan idanunshin nan kan ya ce "Me wannan? Mammi yaushe kika yi lafiyar daukar wata? Watan ma stranger?" Da sauri Afeefah ta miƙe zaune jiri ya kwashe ta ta koma jikin gadon ta jingina idanunta a lumshe zuciyarta na harbawa da tsoro. "Haba Saraki ji yadda ka tsoratata?" Ganin sossai ranshi bai mishi daaɗi ba yasa bata sake cewa komai ba, ya dubi Abeeha "Wawuyar banza come on raka Mammi ɗakinta she should be resting ba stressing kanta ba" Tura baki tayi ya nufeta ta miƙe da gudu ta koma kusa da Mammi sai Harare Harare yake. Mammi tayi dariya "Zan je in huta Saraki don Allah ka yi mata a hankali, she's suffering" Ta dubi Abeeha "kin ga kama ni mu tafi tunda overprotective Yayan naki ya kore mu" In ta shi ne fa tafiya ma zai iya yi mata, itama kuma son da take mishi bata hada da kowa ba, kuma babu wanda ya kaita saninshi don ko kallon abu yayi ta san ma'anar kallon, Dukda fuskarnan ya fi zama a haɗe amma ita tana gane idan yana cikin farin ciki, damuwa ko bakin ciki, yanzu haka ta karanci akwai 'yar damuwa a ranshi sannan har da rigima irin tashi don baya so yaga tana fifita wani a kanshi, su Jannah kan ce Ya Rayyan idan ya samu wacce yake so kamar rai za'a ga kishi kamar hauka. Bayan fitan su ɗakin ya zama shiru sai su biyu kawai hakan ya kara tsinka Afeefah. "Kwanta" Ta ji muryarshi ya daki dodon kunnenta duk da ba da ƙarfi ko tsawa yayi maganan ba. Da sauri ta kwantan tana kara jan bargo, hannunta dake kan cikinta kawai taji sassanyar tafin hannunshi mai taushi ya kama babu shiri ta buɗe idanunta sai suka faɗa cikin nashi da shima a lokacin ya kalleta... **** Ta ɓangaren Sulaiman yana ta gwada Layin Afeefah don ya ji ya jikinta har yamman ya kasa samunta, ya ajiye kila network ne don haka ya cigaba da huldar gabanshi har Magrib baya samunta, yana gama shirin asibiti ya nufi gidan don ya ji ko lafiya baya samunta haka bayan ya isa suka gaisa da su mudi. "Don Allah ko za ku dubo min Afeefah?" Iliya ya ce "Ai Afeefah bata gidan nan, ina zato ma ta barshi gabaɗaya don da akwati ta fita tun safe" Gabanshi ne ya faɗi "wani irin tafiya ba dawowa? An taɓa tafiya haka babu shiri? Gida ta koma ne?" Mudi yace "Wallahi bamu sani ba amma dai kaman gidan dai ba lafiya dai, don Oga saleem ma yanzu haka yana kwance Hajiyar na a hasale, 'yan matan kuma sai kuka Toh ita ma Afeefar da ta fito a chan ta tsuguna ta ci kukanta isashe kan ta tashi ta tafi" Sossai damuwa ya nuna a fuskanshi, idan tunanin shi ya bashi daidai Saleem ya faɗawa Afeefah yana sonta mamanshi ta ji shine suka kore ta, godiya yayiwa su Mudi ya juya ya nufi gida, kila ta koma kauyensu yana ji a ranshi da sauƙi ma tunda har ta faɗa mishi sunan kauyen kan su rabu da bai san inda zai sa kanshi ba, dole ya je ya neme ta. Gida ya dawo Umma na ganinshi tace "Ah Sulaiman ina asibitin? Me ya faru na ga kaman kana cikin damuwa?" "Umma su saleem sun kori Afeefah a gidansu, mamanshi ta kore ta ta koma kauyensu dole gobe in nemi leave in je in sameta ban san ya take ba kuma wayanta baya shiga" "Wacece haka?" Suka ji Muryar Abba! Umma ce ta mishi bayani yana murmushi yace "Toh ai Alhamdulillah! Dama da niyyar aura maka mata na dawo a yau na gama maka uzuri goben da su Yaya Zubairu za ku tafi a yi maka tambaya gabaɗaya tunda Allah ya sa ka samu wacce kake so kuma mahaifiyarka ta gamsu da tarbiyar ta" Murmushi ya saki yana jin sanyi a ranshi Dukda ta wani ɓangaren yana tunanin kar Afeefah taji ba daaɗi tunda bata sani ba kuma ba wai soyayyarsu yayi zurfi bane ita ke ture shi yana sa kai amma dai ya ji daaɗi don da farin ciki ya koma asibitin da bai yi niyyan zuwan ba ya tafi saboda ya samu leave a gobe ɗin don su tafi Dutsen-wai. A waya Abba ya sanarwa yayyenshi biyu akan za'a je wa Sulaiman tambayar Na gani ina so a kauyen Dutsen-wai, basu wani damu ba don duk su burin su ba su hada zuri'a da masu kuɗi ba sai su hada da gidan mutunci gidan tarbiya da sanin ya kamata shi ne abin da suke dubawa. 🖤Gureenjoh🖤 HAIHUWA DA HANJI (A True life story) Fatima Muhammad Gurin (Gureenjoh) Wattpad-Gureenjo6763 Arewabooks-Gureenjoh *FREE BOOK* *Gobe in muna raye sai dare za ku ji ni da yardar Allah* *020* Harara ya sakar mata da sauri ta mayar da idanun ta rufe ruff tsaki ya ja a fili, ya fara ƙoƙarin neman vain ɗinta... 'Asshh' ta faɗa a hankali jin ya soka allurar sai ta fara kokarin janye hannun. "Kina janye hannun nan sai na wanka miki mari akwai wanda yace ki yi ta tuna samarin ki kina kuka har ciwo ya kama ki?" Tsit tayi bata kuma motsan ba, kila Rayyan shine ajalinta wa ya sani don tunda ya daka mata tsawar nan ko numfashi mai kyau ba ta iya ja har ya gama ɗaura mata drip ɗin, bata ji fitan shi ba ita kam tun tana pretending har baccin gaske ya ɗauke ta a haka, don dama jiya ba baccin ta samu ba na kirki gashi yau ta yini a kan hanya tana galantoyi. Sashenshi kawai ya miƙa daga nan don ya matuƙar gajiya hutu kawai yake buƙata, wanka yayi ya fito da alwala ya zo ya shirya cikin wani morrocon jallabiya baƙi sidik mai sheki wanda ya fito da ainihin kyaunshi fatarshi ya haska jallabiyar, masallaci kawai ya wuce bai dawo cikin gidan ba sai da yayi isha, time ya kalla ya ɗauke ido ya nufi cikin main parlorn kai tsaye ɗakin da take ya wuce, ta miƙe zaune bayanta jingine da jikin gadon kafafunta na cikin bargo, idanunta sun kara girma sun dan sauya saboda kukan da ta yini yi ga kuma bacci da tayi tayi, hulan kanta ya zame sosai ya bayyana rabin gashinta mai sulbi, tunani take ya zata yi in ruwan ya ƙare sai taji an yi knocking seconds uku zuwa huɗu ya turo kofan ya sanyo kai da sallama wadda iya shi kaɗai ya san yayi kayanshi. Kanta tayi saurin mayarwa kasa Alamu sun nuna bashi da niyyar magana don har ya zo ya cire ruwan da ya ƙare ya bare wani allura ya fasa yayi mata a canular bai ce takk ba itama bata ce ba, kamshinshi duk ya cika ɗakin har ya gama ya juya zai fita ta furta "Na gode" Bai ce komai ba ya fice daga ɗakin, kai tsaye wurin Mammi yayi, tana daga parlor a zaune cikin kujera abinci ne a gabanta wanda ta gama ci yanzu cikin kula sossai da cimar tata ɗin don professional cooker ya samo mata wacce take kulawa da zallar abincinta kuma take da karatu na musamman akan cimar da ake ba wa masu ciwon ƙoda da kan tafi da diabetes, ba'a so ta ci late kuma da ta gama ta sha magani tana so ya ɗan saketa sai taje ta duba Afeefah. Bai yi magana ba kawai ya zo ya zauna gefenta, ta kalleshi tayi murmushi "Gajiya ne a jikinka sossai Saraki, ka ci abinci sai ka je ka huta" Kai ya gyaɗa kawai don bashi da niyyar magana, da intercom tayi amfani ta kira su a kitchen a kan a kawo abincin Saraki, simple abinci ne marar nauyi yake ci da dare suka kawo suka jere a gabanshi, har lokacin yana kishindige kusa da ita idanunshi a lumshe. "Tashi ka ci kar yayi sanyi babana ko in baka?" Ya buɗe ido a hankali ya ɗan yi murmushi kaɗan sai wani sirrin kyaunshi ya bayyana Dukda murmushin bai jima ba sai dai tabbas duk wanda yayi wa irin murmushin zai jima bai manta ba. Itama murmushi tayi don ita kam akwai fara'a masha Allah, abincin ya ɗan ci kaɗan ya kalleta jin tana cewa "Ina zuwa zan duba Afeefah" Da Kai ya amsa ta fice, ta samu Afeefar ta idar da sallolinta tana kokarin cin abincin da aka shigo mata dashi Abeeha na zaune cikin kujera daya daga cikin huɗu dake gefen ɗakin tana danna waya ganin Mammi ya sa ta taso "Afeefah ɗiyata ya jikin?" Murmushi ta saki a kunyace tace "Alhamdulillah da sauƙi sossai Aunty na gode" "Bana son sake ji kin ce Auntyn nan baki ji Abin da su Saraki ke faɗa bane?" Murmushi tayi. "Abeeha ki kula da ita har tayi bacci zan je Saraki na jirana in na sha sauran magungunan kuma kin san bana iya taɓuka komai sai da safenku" "Toh Mammi sai da safe Allah ya kara sauƙi" "Allah ya baki lafiya sai da safe Mammi" Afeefah ta faɗa ta amsa da murmushi kan ta fice. "Na ga dai baki da niyyar sa abincin nan bari na zuba miki" Abeeha ta faɗa tana zuba mata Afeefar ke cewa yayi amma sai da taji ya mata a ranta kan ta bari kuma tace sai Afeefar ta cinye, sossai moment ɗinta a gidan na yan awannin nan yayi mata daaɗi in ka cire arangamarsu da Rayyan amma Mammi da Abeeha mutanen kirki ne da suka yi ƙarancin samu a wannan zamani. Mammi na komawa ta samu ya gama, ɗaki ta shige ta fara shirin kwanciya cike da dauriya take komai fuskarta dai baya nuna wa amma ita ta san me take ji, sai da ya bata mintunan da yake da tabbacin ta gama yayi knocking ya shiga ɗakin tana zaune bakin gado sanye da doguwar rigan bacci har ƙasa mai kauri, frigde yaje ya ɗauko mata ruwa tulin magungunanta da suke cikin wani basket guda mai kyau ya ɗauko ya zaɓi na daren ya bare ya sanya mata a tafin hannunta, babu musu ta sha yadda ya buƙata kan ta kwanta, ya ja mata bargo ya zauna daga gefenta tare da riƙe hannunta ɗaya. Adu'a yayi ta mata tun tana kallonshi tana danne hawayen da suke ta yunkurin zubo mata har tayi bacci, idanunshi da suka rine ya ɗan rintse yana jin azaban da zuciyarshi ke yi, da yana da yadda zai yi ya mayar da ciwon Mammi jikinshi da bata shekara takwas tana fama da kidney failure ba, da kuɗi za su yi mishi maganin ciwon Mammi da ko zai yi yawo tsirara sai ya samar mata lafiya, sai dai yana roƙon Allah a koyaushe yadda aka bata wa'adin watanni uku za ta mutu amma yanzu shekara har bakwai da abin ya san ba yin su bane ba kuma dabararsu bace Allah ne mai yadda ya so, sai dai a tsananin tsorace yake hakan ya sa sadaqa da duk adu'ar shi yake kan Mamminshi itama saboda rage mishi damuwa take danne wani abin. Sai da ya tabbatar komai intact kan ya fice daga ɗakin yayi Sashenshi, Saleem ya ƙira da har lokacin yana asibiti yana samun kulawa "Har yanzu babu labarin Afeefah ko Rayyan?" Ajiyar zuciya Rayyan ya sauƙe "Na ce ka daina ɗaga hankalinka za mu same ta, ina kan bincike dai in har tana cikin Kaduna ba zata ɓace ba just focus on your health" Kai saleem ya gyaɗa sai yake ganin kaman Rayyan bai yi niyya bane, da yayi niyya ba zai kai zuwa lokacin bai same ta ba, damuwarshi ya zata kwana? A ina zata kwana? Me ta ci? Duk ya kasa kwantar da hankalinshi a gefe ga damuwar rashin ganin mommy Dukda ta mishi abin da ya zama gyambo a zuciyarshi sai dai uwa ce babu yadda ya iya kuma yana ƙaunarta bata da mahadi a wannan duniya. A ɗan sanyaye yayi sallama da Rayyan, Rayyan ya bi wayan da kallo baya jin zai gaya mishi inda Afeefah take saboda yana son Saleem ɗin ya manta da ita once and for all yanzu in ya san tana nan zai cigaba da sa hope a kan samunta alhali mahaifiyarshi bata ɗaura wannan damara ba na mallaka wa yaron nata cikar burin shi hakan ya sa ya ɓoye mishi wanzuwar Afeefar a gidansu. Su Samha ko da suka zo sun ƙaraci zamansu ko ci kanku bai ce musu ba sun gaishe shi ma bai amsa ba, wani irin zafin su yake ji a lokaci ɗaya yana mamaki bai taɓa sanin inhumanity ɗinsu ya kai haka ba, suka gaji suka tafi. **** Washegari Da misalin karfe bakwai na safe Sulaiman ya fito shirye cikin manyan kaya, sallama yayi wa umma tana ta adu'ar dacewa Baba Jummai ma Adu'a tayi ta mishi har ya fice. Gidan Yaya Zubairu ya fara zuwa ya ɗauke shi kan ya wuce gidan babban Yayansu Abban Yaya Ummaru, dattijai ne masu mutunci da kamala kuma duk suna da dukiyar su daidai gwargwadon. Anan suka kama hanyar kauyen su Afeefah yana ta Adu'a da Fatan ya same ta chan Dukda bai yi ma tunanin rashin samunta ba don ina zata koma in ba gida ba? Tafiyan awanni kadan ya kawo su kauyen yana jin hirarsu Yaya Zubairu da suke zaune a baya, sai da suka ɗan shiga cikin garin kan ya ɗan tsaya jikin wani shago matasa ne zaune su wurin huɗu ya sauƙe glass "Assalamu Alaikum barkanmu da warhaka" "Barka dai Alhaji" "Don Allah tambaya nake yi" "To Allah ya sa mun sani" "Gidan su Afeefah kamal" Tsittt suka ɗan yi wannan ya kalli wanchan wanchan ya kalli wanchan.. "Kai ko me zaka yi gidan su Mayyar yarinyar nan? Ai Annoba za ka ce sai mun fi gane ta" "Annoba" Ya maimaita sunan, abin da ta faɗa mishi kenan me yasa ake ce mata annoba? Dan kallon su Yaya Zubairu yayi duk fuskar su ya ɗan nuna mamaki. "Gidansu nake nema" Ya faɗa ba tare da ya ji daaɗin furucin su a kanta ba. "Ka ga kara gaba sai ka tambaya a chan, ba mu san ko laifi ta muku ba kun zo yi wa kawunta tijara abu ya shafe mu lalala bamu shirya rigimar Labaran ba" Babu wanda ya tanka a cikinsu har ya ja motan suka yi gaba, wasu yara 'yan daidai ya samu ya kira su su biyu "Gidan su Afeefah kamal nake nema" Ɗayan ya ɗan kalli ɗayan "Mayyar nan fa suke nema ta gidan su Auwalu" Ɗayan ya zaro ido "Wacce ta cinye Amadun gidan malam yahaya ta gudu duniya?" "Eh ita ce..." Sai ɗayan ya gyaɗa kai ya juya ga Sulaiman da kanshi ya sake mugun ɗaurewa. "Idan kayi gaba ka ɗauki Layin hagu gida na biyu in baka gane ba ka ce gidan su Annoba kake nema ajalin duk wanda ya raɓeki" Suna kai nan suka gudu. "Sulaimanu a wani irin gida ka nemo aure? Wace irin yarinya ce wannan bata da shaida mai kyau?" Shiru yayi shima amsar yake nema don kwata kwata ya kasa fahimtar komai. Gaba yayi don clearing doubt ya sake tambayar wata mata a yanzu annobar shima ya faɗa yana runtse ido aiko ta nuna mishi, Da gaske ne ko wasa? Ya kasa ba kanshi amsa, kaman mafarki yake kaman kuma duniyar halluscination ya shiga don abin ya fi yanayi da almara, wacece Afeefah? Tarin mutane da suka gani kofar gidan kawu ne ya ɗan basu mamaki, bayan yayi parking suka fito su uku suka tsaya suna kallon abin mamaki, dambe ake ci da Kawu da inna larai har kofar gida duk ana tsatsaye ana kallonsu don su in suna yi ba'a raba su in ma ka shiga karshe kai za ka ji kunya, kuma ba karamin dukan ta yake ba, Bakinta ya ƙi shiru duk yaransu na zagaye suna kwasar kallo. "Wani irin tsantsar jahilci ne wannan? Sulaiman a nan gidan ka ɗauko aure? Anya da hankalinka?" Kawu Zubairu yayi maganan kaman ya rusa kuka. Kawu Ummaru ne ya je ya janye kawu Labaran daga riƙon da yayiwa larai ya ce "Haba malam baka san wannan abin da kake yin ya saɓa shari'a ba? Musulmi ne fa kai sannan mutum ba dabba ba wannan ai ɗabi'ar dabbobi ne, ba matarka bace ta sunna?" "Kyale shi ai ni wandon roba nake daidai da kugun kowa, wlh ba zan yi wahala in nemi kudina Labaran ya dinga bin dare yana sace min ba shi ba ciyar da mu yayi ba kuma muyi wahala mu samu ya zama ɓera, Toh ni ba Asabe bace da ka gama kassarata ta koma cima zaune babu abin da take ba, kuma wallahi sai ka biyani kudina" "Ni kike cewa ɓarawo? Yau sai na ci ubanki Larai sai na zubar da hakwaran rashin da'ar nan Malam Sallau shi zai raba mu" Babanta yake nufi, ganin za su cigaba da rigimar su kawu Ummaru ya ja shi gefe. "Ashe baka san Annabi yayi mana hani da dukan matan mu ba? Yanzu kai ba abin kunya bane yaranka gode-gode suna tsaye suna kallon ku ba? Dambe har kan layi? Subhallah" Kwarjini mutumin ya mishi da sai ya yanko mishi magana amma sai ya Buge da cewa "Waye kai? Me kake so? In baka da abin faɗa zan kama gabana don ina da abin yi" Girgiza kai Kawu Zubairu yake Sulaiman kam ya mayar da kanshi kasa yana jin yadda zuciyarshi ke cigaba da tsitstsinkewa don tabbas da matukar wuya Su kawu su bari su yi surkuntaka da mutum irin kawu, yanzu wannan baban Afeefah ne? Innalillahi wainna ilaihi rajiun ya maimaita ya kai sau biyar. "Sunana Umaru Malami zuwan namu ya shafi 'yar wurin ka Afeefah" Zaro ido kawu yayi "Ba dai a yawon tambaɗarta ba ne ta kashe muku wani kuka zo nemanta? Ni fa na jima da yanke alaqa da yarinyar chan ba zai yiwu a dinga zuwa ana ɗaga min hankali akan kashe- kashe da take ba" "kashe-kashe?" Kawu Zubairu ya maimaita "Wai baku sani ba? Ai rikakkiyar Mayya ce da ta addabi al'ummar garin nan a ƙarshe korinta muka yi ta shiga duniya" Jiri ne ya kwashi Sulaiman yayi baya baya ya dafa mota, zuciyarshi na harbawa da karfin gaske tuni idanunshi suka sauya, kwalwarshi ya nemi tsayawa da aiki amma sai ya tuna farkon abin da ya kawo Afeefah asibitin su ta sha poison ne don ta kashe kanta! Afeefah tana da tarin damuwa da yake haddasawa jininta sauƙa sossai zuciyarta kuma na ta kokarin samun matsala, me kenan? Menene ke kunshe a rayuwarta haka? Duk ya rikice amsa yake buƙata sai dai ba daga bakin wannan kaskantaccen mutumin da ya kira kanshi kawunta ba. "Toh mun gode ko, sai anjima" Juyawa kawu yayi ya kada rigar shi yayi gaba. "Sulaiman wannan ƙasƙanci har ina? Yanzu inda ka zabi neman aure kenan? Toh ba'a zuriyar Malami ba" Kawu Zubairu ya faɗa yana bude mota ya shiga, kawu Ummaru ma ya shiga Sulaiman da kyar yayi composing kanshi ya zagaya ya shiga ya tada motar a hankali yace "Don Allah ku yi haƙuri kawu ku yi min uzuri, wallahi Afeefah ba haka take ba ita nake so ba kawu..." "Sulaiman ko Afeefah ta fi kowa musulunci a duniya ba za mu nema maka aurenta ba, ba za.mu taɓa hada zuri'a da irin mutanen nan ba, ban damu don an ce mata Mayya ba duba da irin kauyen da tarin jahilci ya musu yawa amma a yadda ta shiga duniya danginta suka watsar da ita har suke ikikarin yanke duk alaqa da ita, da kuma yadda muka sami wannan gida ba gidan aure bane, kana da tarin mata masu nasaba da asali cikakku waenda suke gaban iyayensu zaune don haka ka tabbatar baka kara tado zancen wata Afeefah ba, a yau ka fara dubawa cikin sauran yaran da iyayensu suke maka tayin auren su za'a hada aurenka da Munir" Kawu Ummaru yayi maganan. Muryar shi na rawa ya ce "Amma ka..w..." 🖤Gureenjoh🖤 HAIHUWA DA HANJI (A True life story) Fatima Muhammad Gurin (Gureenjoh) Wattpad-Gureenjo6763 Arewabooks-Gureenjoh *FREE BOOK* *Ina so na yi addressing wani issue, na yi kokari in share in yi kaman ba komai amma dai na kasa, wato muna zuwa wani mataki da za'a iya fara cewa Gureenjoh na wulakanci ban damu ba saboda Allah ya gani ba wulakancin nayi ba, babu yadda za'a yi na fara littafi na yi nisa ki zo ki ce in tura miki na amsa na kuma tura miki zuwa inda na tsaya, muna groups dayawa dake da nake posting a maimakon ki cigaba da tarawa ko ki cigaba da bi baki yi hakan ba bayan kwana biyu na sake yin nisa ki sake dawowa ki ce in kara tura miki daga inda na tura miki last zuwa inda na tsaya wallahi ba zai yiwu ba, ba zaman banza nake ba wani lokacin ni na san yadda nake squizing time ɗina ina typing, wallahi ba zan tura ba idan za ki jira na gama na haɗa document na tura groups ki gani ki karanta fine, idan ba za ki karanta ba duka a wurina daidai ne* *jama'a kuyi haƙuri da Page nan guntu ne pls, idanuna rufewa su ke da kyar na kai inda na kai saboda gajiya da bacci* *021* "Sulaiman?? Har za ka ja da maganan Yaya a kan yarinyar? Aaa lallai, yo ko mahaifinka ya isa ya sauya maganan nan?" Kawu Zubairu ya katse shi a hasale. Shiru Sulaiman yayi sai dai idanunshi tamkar garwashi, zuciyarshi yake jin ya wani matse ya mishi nauyi wane dutse aka ɗora mai, kawai don kawu bai da hali sai a hana shi auren Afeefah? Me laifin ta? Ita me tayi? Har suka shigo Kaduna bashi da natsuwa, da kyar ya kai kowannensu gida suna ta kushe wannan neman auren nashi haka ya nufi gida ko da ya shigo a parlor ya samu Umma, ganin yanayinshi kaman zai faɗi ta miƙe da hanzari ta riƙe shi "Sulaiman! Menene? Lafiya kake kuwa? Ko wani abin ne ya samu Afeefar?" Girgiza kai Yayi yana neman inda zai zauna ta ja shi kujera suka zauna tare, Baaba jummai ma da tun safe take ta adu'ar dacewa ta fito, ruwa ta je ta ɗauko mishi Umma na tsaye kanshi tana ta tambayar shi duk ta rikice ta sanshi da masifar migrine in ya fara kuma baya jin magani, ruwan ya karɓa ya sha sossai tamkar zai fasa ihun kuka yace wa Umma "Umma wai su kawu ba za su nema min aurenta ba, wai ba za su hada zuri'a da ita ba, Umma idan kenan kawunka bashi da halin kirki sai aka ce kaima haka kake? Me Afeefah tayi na kin aurenta? Don Allah ki yiwa Abba magana ya samu Yayanshi zan nemi Afeefah! Zan neme ta duk inda take ni dai don Allah ya bar ni in aureta a haka nake son ta" Duk sun kasa gane inda ya dosa, Abba da shigowan shi kenan ya ce "Ba da Miyau na ba kam, sai dai kuma idan kai zaka nemawa kanka aure wannan kam zaka iya amma tunda har Yaya ya kirani ya tabbatar min gidan chan ba gidan neman aure bane ba zan taɓa sake tado maganar ba don na san ba karya ya yi ba, da kai aka je ai ba da wani ba kuma kaima shaida ne" Idanun da suka sake rinewa sossai ya zubawa Abban yace "Abba ita wallahi ba haka take ba, nitsatsiya ce kuma tana da tarbiya daidai gwargwado, Abba aka auri karuwa da ta tuba ma bare Afeefah? Abba ko ladarta ba za ka bari na samu ba? Korinta fa suka yi bayan sharri da ƙage da aka lankaya mata a garin" A yanzu kam hawaye sai da suka zuba mishi. "Ko ma menene Sulaiman ba a zuri'ar mu ba, ban taɓa saɓa maganan Yayana ba kuma ba zan fara a kan ka ba Sulaiman, ku fara shirye-shiryen auren shi za'a hada da na Munir" Umma ta ɗago da sauri ta kalleshi "Alhj wata ɗaya fa kacal ya saura na Munir yaushe ya gama warke wannan ciwo da zai yi aure?" "Ke kenan kike goya mishi baya yayi abin da yake so ko? Toh shikenan kar yayi" Yana kai nan ya wuce abin shi. Baaba jummai kam har hawaye take yi, bayanin abin da duk ya faru yayi musu bayan ya gama ya kama hannun Umma "Don Allah umma ko auren za'a yi min ki taimaka ki saka baki a hada da Afeefah wlh ina son ta, tausayinta kuma yanzu ya sake kama zuciyata har ina jin kaman zai fashe" Duk sun tausaya mata, Baaba jummai ta sha kuka sai Allah ya isa take yi a madadin ta, abin da ya dame su ma kasancewar yanzu ba'a san inda ta dosa ba. "Yanzu ka je ka sha magani ka huta sai ka je ka nemo mana ita in har muka sameta komai mai sauƙi ne, rayuwar 'ya mace a haka hatsari ne komai zai iya faruwa, imma a yi mata mugun abu ko kuma ta jefa kanta halaka" Duk sun gamsu, Miƙewa yayi ya nufi Sashenshi cike da tunanin ta ina zai fara nemanta? ***** Saleem a Washegari aka sallameshi ya koma gida, shi ne ma ya matsa saboda ya damu da halin ko in kula da Mahaifiyarshi ke mishi, ƙannenshi kam ba ya kula su bayan ya dawo wanka yayi ya fito, har kicin ya shiga Talatuwa ta bashi abinci ya zo ya ci kan ya nufi ɗakin Mommy, sossai yake kokarin danne damuwar da yake ranshi saboda Rayyan da yayi ta ƙoƙari wurin ganin ya manta Afeefah ya cire ta a rayuwarshi. Zaune ya sameta bakin gado tana danna waya, sallamar shi kawai ta amsa amma ko ɗago ido bata yi ta kalleshi ba, a gaban kafafunta ya je ya zauna "Ban taɓa tunanin akwai ranar da zai zo da zan yi rashin lafiya har in kwanta na tsawon kwana daya gadon asibiti Mommyna bata zo ta duba ni ba, na san na miki laifi mai girma ne shiyasa na kasa bari in samu lafiya na nemi a sallameni don in zo in nemi yafiyarki, kiyi haƙuri in shaa Allahu na cire Afeefah daga raina..." Ya faɗa a raunane "Duk kuma abin da kike so zan cigaba da so matukar bai saɓawa shari'a ba ko da kuwa zai cutar da ni ne, ki yi haƙuri Mommy" Ɗagowa tayi ta kalleshi sai zuciyarta ya karye, wani sashe na cewa bata yi mishi adalci ba, wani kuwa na bata ƙwarin gwiwa a kan abin da ta aikata ɗin ai taimakonsu ne gabaɗaya. "Zan yafe maka in manta irin rashin kunyar da ka yi min matuƙar ka bi umarnina na karshe a gareka" Ta faɗa cikin tabbatarwa. "Mommy ko me kike so ki faɗa ni kuma zan cika miki ko da bana so" "Zan aura maka Sabreena nan da wata guda" Da sauri ya ɗago ya kalleta amma sai harshen shi ya mishi nauyi, uffan ya kasa cewa sama da mintuna uku kan ya ce da kyar "Allah ya sa hakan shine mafi alkhairi" "Ita ce ma Alkhairin naka" Kai kawai ya gyaɗa ya miƙe ya fice fuskar shi babu walwala sam, a parlor ya ga Sameera na zaune, ido ya ɗan zuba mata ganin ta mishi rama kuma ta yi zuru zuru ga damuwa nan fal a fuskarta, kaman zai yi magana kuma sai ya wuce abin shi. **** Ta ɓangaren Afeefah ta tashi Washegarin jikin da kwari sossai, wanka tayi ta saka kayanta ta samu wuri ta zauna don bakunta ne fal cikinta da kuma tsoro, har yanzu Mammi bata san wacece ita ba shin wani abu zai chanza in ta san wacece ita? Anya shi ma Rayyan ya san wacece ita kuwa? Tunanin da yake ta kai komo kenan a ranta har ta ji an tura kofan an shigo. Ɗaga kai tayi tana amsa sallamar Abeeha. "Alhamdulillah jiki yayi sauƙi sossai Aunty Abeeha" Ta amsa mata bayan ta jefa mata tambayar yaya jiki, Zaro ido Abeeha tayi "Lallai Afeefah ni ce Auntyn taki? Kin ga kirani Abeeha na bana wani son Aunty na san ko da zan girme ki ba zai wuci da shekaru biyu ba" Afeefah ta ɗan yi murmushi "Toh ai ko da kwana ɗaya ne kin cancanci na ce miki hakan bare har shekaru biyu" "Ni dai bana so na bar miki" Ta faɗa da dariya, Afeefah ma tayi murmushi "Kin karya kuwa?" Abeeha ta tamabaya don ita ta tafi lectures 6 yanzu kenan dawowanta 9 ɗin nan. "Eh sun kawo min har nan na karya, ina dai so in je in duba jikin Mammi ne kuma ban san ta inda zan ganta ba" "Nima chan nayi daga nan, na fita duk kuna bacci. tashi mu je" Miƙewa Afeefah tayi Abeeha na cewa rigarta ya mata kyau tayi murmushi tana mamakin saukin halin Abeehar da saurin sabon ta. Sai kallon gidan Afeefah ke yi tana ƙara yabawa abin da ya fi burgeta yadda ko ina kalkal sai kamshi da sanyin Ac ke tashi, ga nan chandliers design daban daban masu kyau kowanne da kalar hasken shi da tsaruwarshi, silifas ɗin kafafunsu mai taushi kaman ka nitse ciki take ta jin daaɗin shi don duk basa yawo kafa banza a cikin gidan da lofas ɗin su masu kyau itama kuma har ɗaki aka kai mata saboda sanyin tiles, ɗakin Mammin suka tura da sallama suka shiga. A kan kujera suka samu Mammi gabanta fruits ne masu low potassium tana sha shima kuma in portion ne akwai yawan da ba zai yiwu ta sha ba, Daga kan gadonta Rayyan ne yana cikin bargo Dukda ba bacci yake ba idanunshi lumshe yana tunanin maganan da Mammi ta gama faɗa mishi yanzu, numfashi ya ɗan sauƙe ya buɗe idanunshi ya kalli inda suke a lokacin Afeefah ta kai ƙasa Mammi na ce mata "Tashi! Tashi a ƙasan nan Afeefah ga kujera zauna ko ki zauna bakin gado ina ke ina zaman wannan sanyin" A bakin kujera ta ɗan dosana tana gaishe da Mammin, Mammin ta amsa cike da kulawa tana tambayarta jiki ta ce ta ji sauƙi, Abeeha ma ta gaisheta tana tambayar karfin jikinta duk adua suka dinga yi wa Mammin tana amsawa, sam Afeefah bata kula da Rayyan ba Mammi da ta kosa ta ji Afeefar daga ina take kuma ina danginta tace "Afeefah ki yi haƙuri da tambayana, ba wai zan tambayeki bane saboda mun gaji dake ko muna so ki tafi ba, yana da kyau ne tambayar saboda mu san asalinki mu san me ya rabo ki da danginki, in kika duba yadda wannan zamani ya zama har wasu tsoron taimakon suke saboda dayawa an fi janyo su inuwa su tura mutum rana. Idan har baki shirya sanar da mu ba kuma za mu hakura mu cigaba da zama dake har ki ji kin gamsu kina son sanar da mu ɗin. Na yi ta tambayar Saraki bai ce min komai ba" Afeefah ta ɗan muskuta gabanta na tsananta faɗuwa ta ce "Mammi don Allah ki daina ba ni haƙuri, ya zama dole in sanar da ku wacece ni! Ina tsoron saka ki cikin damuwa alhali ba lafiya ce ta ishe ki ba don labarina bashi da daaɗi, bashi da abin burgewa ko karsashi, babu abin da ke ciki sai tarin baƙin ciki, kuka da damuwa, Mammi Sunana Afeefah kamal na buɗi idona ne kawai na tsince ni gaban kakata wacce ta haifi babana...." A hankali ta cigaba da basu labarinta tun daga farko har ƙarshe, ta gaji da kuka a kan labarinta hakan ya sa a yanzu ta danne kwarai bata yi kukan ba sai idanunta da suka rine matuƙa gaya, bayan ta gama ta ɗago ido tana kallon expression na su Mammin gabanta na faɗuwa zuciyarta na duka da ƙarfin gaske.... 🖤Gureenjoh🖤 HAIHUWA DA HANJI (A True life story) Fatima Muhammad Gurin (Gureenjoh) Wattpad-Gureenjo6763 Arewabooks-Gureenjoh *FREE BOOK* *22* Ga dumbin mamakinta dukkansu biyu kuka suke yi, Abeeha kam ma da sauti yayinda Mammi ke zubar da hawaye, ko kan tayi wani yunkuri Mammi ta miƙe ta iskota ta ɗago ta sai ta sanya ta jikinta ta rungume tana shafa bayanta, wannan dalili! wannan ɗumin jikin shi ya saka Afeefah fashewa da sassanyar kuka mai sauti. Sun fi mintuna goma a haka tana wannan kukan, tuna komai take yi tamkar yanzu ne ya faru ji take duk mace-macen yanzu ne suke dawo mata sabo, taji tana kewar mahaifiyarta da Aunty zee, wannan tausayi da kauna da ta gani daga Mammi sai ya tsaya mata a rai ta ji itama tana ƙaunar matar tamkar mahaifiyarta. Rayyan da tun kan tayi nisa ya lumshe idanunshi bai buɗe ba sai da ya ga kukan na yawa, duk tsikar jikinshi jinshi yake a tashe, ko da ya miƙe zaune sai da ya ji kanshi ya sara ya ɗan runtse idanunshi ya buɗe kan ya ja tsaki ya sauka daga gadon, ya taka ya dafa kafadar Mammi da har lokacin take rike da Afeefah. Mammin gabanta ya faɗi tuna yana ɗakin ta tuna labarin Afeefah sai tayi sauri ta saki Afeefah ta waiga tana kallon yanayinshi, idanunshi ya sauƙe kasa a hankali yace "Mammi please ki bar kukan nan, you are sick already kukan nan bashi da amfani, dole ne sai mutum ya rayu da dangi? Dole ne sai sune kaɗai za su baka farin ciki da kulawa? Na Allah na nan dayawa Mammi..." Yankewa maganan yayi ya ɗago garin kaucewa idanun Mammi sai nashi suka sarƙe cikin nata, sama da seconds huɗu yana kallonta kan kawai ya juya ya bar ɗakin. "Saraki.! Saraki....!!" Bai juyo ba ya fice, ta duƙar da kanta tana ambatar sunan Allah... Chan ta sauƙe numfashi ta waigo ga Afeefah da tunda taji sauƙar muryarshi da yadda yake magana da amo kukanta ya tsaya chakk, haɗa idanun da suka yi ya matuƙar Dakar zuciyarta idanunshi abin tsoro ne a gareta amma a yanzu sai taga ya zama wani iri duk yadda zata fassara ma'anar kallon nashi ta kasa, maganan Mammi ne ya dawo da ita tunaninta. "Lallai Afeefah kin ga rayuwa, haƙiƙa na kaɗu da labarinki abin mamaki kika iya daurewa kika cije kika tsallake wannan jarabawa duk da kananun shekarun ki, Afeefah rayuwar nan duk jarabawa ce kuma ko wani lokaci yana da karshen sa, za mu yi ta shan wahala a duniya amma sakamakon yana hannun Allah kuma ya fi jarabtar wanda ya fi kauna daga cikin bayinsa, Afeefah ina so ki san idan dai har ni, Abeeha, jidda ko Saraki muna raye a wannan duniya kin gama kuka, zan cigaba da rikeki har karshen numfashi na haka zan yi musu umarnin cigaba da kula da ke da baki kariya har nasu karshen numfashin, in shaa Allahu kin gama zubar da hawayen baƙin ciki Afeefah... Sannu! Sannu da juriya" Sabon hawaye ne suka cigaba da silalo mata ta sake rungume Mammi tana fashewa da kuka, Abeeha ta taho ta ɗago ta tana riƙe hannunta "In shaa Allahu ba za mu taɓa kyamatarki ba Afeefah ai duniya ce idan wani ya ƙi ka dole wani ya so ka haka Allah yayi rayuwar, ni na yarda ki ƙirani Addah don ko kowa zai guje ki in shaa Allahu ni ba zan taɓa gudar ki ba" Sossai take kuka, a ranta Adu'a take tana tuna irin kaunar da Aunty zee ta nuna mata a ƙarshe ta tafi ta barta, anya ta zama mai adalci? Anya zamanta a gidan zai haifar da ɗa mai ido? Karshen wahalar kenan ko kuma akwai saura? Duk ta bar wa Allah. Sossai suka rarrasheta ta natsu kan Mammi ta miƙe tayi sashen Rayyan don duk yana cikin ranta tun ɗazu, a kwance ta same shi hallau dai idanunshi a lumshe, kai tsaye ta je ta sa hannu a goshinshi ganin jijiyoyin kanshi raɗa-raɗa a waje, jin hannunta ya sa ya buɗe idanun da suka sake sauyawa ya zuba mata "Saraki ciwon kai ne? Ko za ka je asibiti?" Girgiza kan yayi kaɗan yana yamutsa fuska "Ba sai na je ba Mammi" "Saraki in na barka haka dare ba zaka iya bacci ba, ka taimakeni ka je ka ga psychiatrist din ka" Shiru yayi bai ce komai ba. Ta sauƙe numfashi ta fara duba wayanta cikin mintuna kaɗan sai ya ji muryarta tana magana da likitarshi, buɗe ido yayi ya kalleta bata damu ba har suka gama wayan. "Za ta zo, don Allah ka tashi ka saka wani abu a jikinka mu je parlor" Ta faɗa cikin kulawa kaman yadda yake damuwa da ciwo da damuwarta, shi ma bai san yadda zai yi bane, bai san ya zai yi ya hana kwakwalwarshi tsayar da tunanin baya ba, bai san ya zai yi ya cire tsananin nauyi da damuwar da ke kwance a ƙasan ranshi ba, a duk lokacin da ya samu sassauci to fa a tsakanin da yake ganin farin ciki da walwala a fuskar Mamminshin ne saboda baya so yake sakata cikin damuwa amma yaya zai yi? "Zan zo!" Ya faɗa a hankali. Ta juya ta fice da damuwa a fuskarta, bai yi bacci ba a daren jiya dama ya saba da rashin isashen baccin dare, tun tana kwana dashi har taga yayi girman da bai kamata su cigaba da kwana ba amma ko bacci take tana tunanin yadda yake tafiyar da nashi daren, ba'a yi mishi adalci ba amma kuma to ya suka iya ne? Da kyar ya miƙe ya saka armless vest mai fadi da three quater da ya kai mishi gwiwa, a bakin gadon ya zauna yana dafe kai har lokacin fuskarshi jazir babu ɗigon fara'a a kan fuskar tashi, ba'a jima sossai ba sai ga Mammin ta dawo ta kama hannunshi suka fito, a zaune kan kujera ya ga Dr. Ɗin tashi macece babba da a haife zata haife shi, ganin sun haɗa idanu ya sa tayi mishi murmushi ya ɗauke idanu, ajiyar zuciya ta sauke har ya zauna ya kishingida ya ɗaura kafa daya kan daya Mammi ta fita bata ce komai ba. "Malam Rayyan! Barka da warhaka" Ido ya ɗan buɗe ya kalleta kan ya amsa. "Whats happening? Na zaci mun wuce wurin nan duka..! Mafarkin ne?" Shiru yayi chan dai ya gyaɗa kai "Am having a sleepless night for almost a month now" "Me ya faru? Are you taking your pills?" Gira kawai ya ɗaga don kan ya mishi nauyin da ba zai iya dagawa ba. Ba don ma ya san darajar likitar ba ba zai kula ta ba, tayi ta janshi da magana dai har ya ɗan sake ta bashi magani cikin kulawa da kwarewa a aiki. "Mammi wants me to get married, tana tsoron ta mutu...." Ya ɗan yi shiru zuciyarshi babu daaɗi sam kan ya cigaba "ba ta so ta bar ni ni kaɗai ba tare da mata ba and i hate the idea... Me yasa take yawan zancen mutuwa? Yana damun zuciyata da kwakwalwata kina tunanin zan rayu bayan bata nan?" Idanu ta zura mishi, Rayyan a cikin patients ɗinta da take gani sama da shekaru talatin yana daga cikin na daban da take jin damuwarshi tamkar ɗan cikinta, tana tsananin tausayinshi gashi kuma Allah sai ya sake aiko mishi wata jarabawar akan wata na rashin lafiyar Mammi da fargabar mutuwar a kowani lokaci, sam bata so Mammin tashi take kawo mishi zancen tunda a ranshi ya riga ya san kowa zai mutu idan ajalin shi ya zo amma kuma ta taya ta duba raunin da yake danne wa a cikin zuciyarshi he was already traumatized, yana fama da insomia for so long ciwon Mammi kuma ya haifar mishi da anxiety tsoro da fargabar barin shi da zata iya yi. Lallaɓa shi tayi tayi har ya ɗan sake, maganin da ta bashi kuma ya taimaka mishi don kafin ta tafi ma yayi bacci a kan kujerar, Mammi ta samu "Don Allah Maman Rayyan ki taimakeni a kan Rayyan, ki daina mishi maganganun da zai ji a ranshi kaman wasiyya ne, kin san matsalar shi kin san da ya ya girma in ba Allah ba babu mai iya kawo Rayyan matakin da yake kai yanzu" "Dr. Ya zan yi ne? Ina faɗa mishi hakan ne saboda ya shirya, ya kamata ya shiryawa hakan dole zata kasance amma bana Fatan hakan ya kasance bashi da wani kafaɗar, bana Fatan hakan ya kasance ba shi da inda zai iya bayyana damuwarshi shiyasa nake so yayi auren" "Amma kin san matsalar da niyyar auren nan ya jawo a baya, a maimakon ya gyara sai tabargaza da yayi mana har ya zama for months Rayyan baya aiki baya kuma fita ko ina, bakya tsoron abin da ya faru ya sake faruwa?" Shiru Mammi tayi itama duk damuwa a kan fuskanta kan ta ce a hankali "Zan san yadda zan yi likita, na gode sossai da taimakon ki ina fata zai ɗore ko da bana nan" Murmushi kawai tayi ta taso ta dafa kafadar Mammin ta ɗan bubbuga kan ta fice bata iya ta ce komai ba. Hawaye ne ya silalowa Mammin, ita kadai ta san me take ji, ita kaɗai ta san tsoro da fargabar da bawa kan shiga a duk sadda aka ce maka ga wa'adin mutuwarka Dukda bata yarda ba amma hakan ya tsaya mata a rai tun shekaru bakwai baya, Dukda ta wani gefen hakan ya matuƙar bata kusanci da ubangijinta sai dai tsoronta yadda zata tafi ta bar Rayyan, bata jin yaranta matan saboda basu da matsalar komai amma Rayyan fa? Raunin shi sabo zai dawo bata son hakan bata Fatan hakan don haka dole ne a gareshi ya nemi abinda zai tallafeshi a bayanta. **** Ta ɓangaren Dr. Sulaiman neman duniya ya saka an yi wa Afeefah sai dai babu ita babu alamunta, police station har uku daban daban ya kai report sai dai babu ko duriyarta. Tun yana ciwon kai a tsatsaye har sai da ya kwanta don da gaske ya matuƙar damuwa, a ƙarshe haƙuri umma tayi ta bashi akan ya fawwalawa Allah ya karɓi auren da aka bashi don Abba ya nuna mishi babu gudu babu ja da baya. A dole daga ita har ƙannenshi suka fara shirye shiryen auren tunda sati biyu kachal ya saura a yanzu. **** A ɓangaren saleem ma duk ya ƙare a tsaye saboda damuwa da tunani, a kullum adu'ar shi a kan Afeefah ne Allah ya tallafeta ya hanata faɗawa halaka Allah yayi riƙo da hannayenta ya bata uwar ɗaki na ƙwarai, har yanzu iya gaisuwar ƙannenshi kawai yake amsawa wanda abin ya dame su sossai ya zura musu ido kawai musamman mommy da ke ta shirye-shiryen aure ka'in da na'in ita uwar amarya kuma uwar ango. Sameera na zaune a kan plastic chair a wurin parking lots saleem ya shigo da motar shi ya zo yayi parking ya sauƙa, bai mata magana ba don ta gaisheshi da safe kuma ya amsa har zai wuce tace "Yaya!" Ya juyo ya kalleta duk tayi wani iri da ita "Yaya don Allah kayi hakuri da abubuwan da muka yi maka, wallahi na gane kuskurena tun da jimawa na tuba don Allah" "Me kuka yi min Sameera? Ai ni dan uwanku ne ba zaku iya min komai ba ko? Sai bare ne zaku iya yi wa... Babu komai Allah yana gani" Kuka sossai take yi. "Allah ya riga ya nuna min iyaka ta ko a haka na gane kuskurena, Yaya in na tuna abin da muka yi wa Afeefah sai Naji tamkar jayayya muka yi da ubangiji... Za ka yi mamaki yaya idan na ce maka na san abin da kake ji a ranka, na san zafi da raɗaɗin rashin masoyi domin Allahnta ya saka mata, a sadda take nan ina samun sauƙi ne kawai da kallonshi amma a yanzu ko arzikin kallon babu tunda Afeefah bata nan haka kawai ba sakayya bane?" Idanu ya zura mata duk ta zama wani iri ta rame, "Sameera wa kike so? Rayyan?" Ta girgiza kai "Sulaiman?" Tayi shiru ya ɗan yi jimmm, kan ya matso ta. "a haka kawai Allah ya barki ya rama mata, ba yafiyata za ki nema ba ita za ki nema ta yafe miki" Yana kai nan ya juya ya fice. Ta saukar da kai tana hawaye, tana bibiyar Sulaiman sossai Dukda bai sani ba a haka ta san auren shi wadda hakan ya sake daga mata hankali amma ya zata yi? Jarrabawarta kenan, ashe Afeefar ma ba laifi tayiwa ubangiji ba ya zaɓi jarabtar ta ta hanyar da ya so, ba zata taɓa cewa Sulaiman tana son shi ba amma zata yi Adu'a Allah ya sassauta mata ya kawo karshen shi. **** Rayyan yayi kwana biyu yana jinya kan ya ɗan sake Dukda ba sossai ba, sam ko a hanya basu sake haɗuwa da Afeefah ba don bata zauna ba shima kuma ba shiga mutane yake yi ba idan bashi da lafiya, Abeeha ta ɗauke ta suka yi sayayya sossai wadda Mammi ce duk tayi mata, suka je aka sama mata makaranta sun ma ƙi karbar ta sai da kyar aka barta SS1 za ta yi waec kawai SS2, idan tace hankalinta ya taɓa kwanciya irin na kwana biyun nan tayi ƙarya, wani irin so da kulawa suke nuna mata. Bata aikin komai don gidan ma'aikata har sun yi yawa sai ka ga daman zuwa kitchen, uniform da ake jira ɗinka mata bai samu da wuri ba saboda uniforms ɗin school din ba'a Kasar nan ake yi ba kuma tsakiyar term ne ya ƙare already wanda suke dashi ba'a kawo wani ba, don haka kullum suna tare da Abeeha kusan duk wanda ya san Abeeha sai ya san Afeefah matsayin 'yar uwarta. Gidan Jannah suka je suka sha yinin su itama bata da damuwa kaman dai Abeeha don duk sun samu nagartaccciyar tarbiya daga mahaifiyarsu. A yau monday Afeefah ta fito sanye da uniform ɗinta mai dauke da bajin KIS(Kaduna international school) tayi kyau sossai a uniform din sai kuma tayi kankanta, murmushi ne sossai fuskarta tana yiwa Mammi sallama Abeeha ce zata sauketa in an tashi sai Driver ya je ya ɗauko ta, har tana shirin fita Mammi tace "Afeefah kin mance lunch box ɗin ko kunyar dauka kike?" Abeeha tace "Ana kunya da ciki ne? Oya maza yi sauri ki sameni a mota" Da sauri ta juya bata ankara da akwai mutum ba kawai ta ji ta buga goshinta a kan kirjin shi, kamshin turarenshi ya sanar da ita waye tun bai ɗago ba a razane tayi baya baya tana ɗago ido sai suka sarƙe cikin nashi fuskar nan tamau, uban Harara da yake zabga mata ya sa ta nemi rikecewa... "Ba ki da hankali ne? Ko ba kya abu da natsuwa ne?" Dakakkiyar muryarshi ya sauka a cikin kunnenta ai sai.... 🖤Gureenjoh🖤 HAIHUWA DA HANJI (A True life story) Fatima Muhammad Gurin (Gureenjoh) Wattpad-Gureenjo6763 Arewabooks-Gureenjoh *FREE BOOK* *23* "Ba ki da hankali ne nace!" Ya sake faɗa da ɗan ƙarfi, in za ta iya tunawa kalaman shi na farko kenan a gareta, kila to bata da hankalin ne don yanzu ma rikice wa tayi ta rasa me zata ce Bakinta ya kasa furta ko A sai baya baya da tayi da sauri idanunta da suka firfito farare tass a kanshi. Ganin Hararar da ya watsa mata yana cewa "Daina kallona!" Ya sa tayi saurin ɗauke idon, Mammi ce ta ceceta "Haba Saraki! Bata san kana wurin bane za ka tasa ta gaba kana zazzare mata ido, kayi haƙuri" Mammi yake kallo, itama Afeefah jin abinda Mammi tace ya sa tayi ƙoƙarin har haɗa kalaman haƙuri tace "Ka..yi haƙuri" Tsaki ya ja ya wuce ta ya barta da fitinannen kamshin shi, kitchen ta wuce ta ɗauko lunch box ɗin mai kyau dashi ta fito a sanyaye tacewa Mammi "Mun tafi Mammi" Daga haka ta fice a parlorn da sassarfa don tana fitowa ya zuba mata ido, tsaki ya ja bayan fitan ta ya dubi Mammi "Meyasa kuka sakata makarantar da ba'a sa hijab kamar ba musulma ba?" Mammi ta kalleshi "Yanzu menene aibun uniform din nan?" Sky blue shirt ne da navy blue blazer da skirt Dukda a gwiwa ne sai dai ta saka socks da ya haura mata har cinya, cover shoe Black ne kafafunta sai navy blue cap da ta rufe kanta kirip dashi, neck tie ne me layi layi sky nd navy blue sun yi mata kyau kayan kuma babu inda ke bude jikinta banda hannayenta da fuskarta. Baki ya taɓe bai sake cewa komai ba, abin kari mammi ta kira aka kawo mishi ya fara karyawa a hankali, bayan ya gama ya dube ta "Mammi auren salim next week friday" "toooh aure haka kwatsam babu sanarwa babu shiri?" "Nima jiya ne yake faɗa min" "Toh Allah ubangiji ya sanya alkhairi ya sa da mu za'a yi" Ya amsa da Ameen. Daga nan wani hirar ta shiga yi mishi yana bata amsa a hankali hankali har suka gama ya miƙe ya bar gidan. Ƙarfe biyu sai ga 'yan makaranta an shigo, bata samu Mammi a babban parlor ba kawai sai ta shige ɗakinta tayi wanka ta sauya kaya zuwa doguwar riga Abaya onion colour mai kyau, hula ta saka ta fito ta nufi ɗakin Mammi jinta take very fresh nd healthy, wani sa'in ta kan tuna salim da halin da yake ciki sai kuma tace kila ma ya manta da ita, Sulaiman ma kan zo mata rai ko yaya yake oho bata sani ba. Da sallama ta tura parlorn Mammi ta shiga ta sameta zaune gabanta abinci ne, farin shinkafa ce basmati aka dafa amma dibawa aka yi kaman na jinjiri da alama ma da measurement cup aka gwada don ba zai wuce 1/2 cup ba, sai wani wake green, akwai salad ɗan kaɗan shi ma daga lettuce sai cucumber da lemon tsami, kaza ce gasashiya 'yar kaɗan itama a gefe sai ruwa. Murmushi Mammi ke yi tana amsa sallamar "Barka 'yan makaranta an dawo?" "Eh Mammi mun dawo, ya jikin?" "Alhamdulillah, Ki karɓi abinci ki ci sai ki huta ko?" "Toh Mammi" Abincin Mammin ta zubawa idanu sama da seconds biyu kan tace "Mammi idan ba damuwa zan iya tambayar me yake damun ki?" Mammi tayi murmushi tace "Babu damuwa Afeefah, ciwo biyu ne ke damuna an haifeni da diabetes na gado don tun ina shekara biyu aka gane cewa na gaji ɓangaren mahaifina ne da ciwonsu na sugar, matsalar ciwon sugar idan yayi tsanani yana iya affecting koda to wannan dalilin ne ya janyo na samu damuwa da koda shekaru tara zuwa goma baya, an ma yi min aiki an chanza duka ba'a dace ba Afeefah har ma an ba ni wa'adin wata uku shine ƙarshen rayuwata sai kuma gashi da yardar ubangiji na shekara bakwai bayan nan" Afeefah damuwa ne sossai ya nuna a fuskarta tace "Toh Mammi shi ciwon ƙodar yaya yake? Ba'a warkewa ne?" "Allah ya halicci mutane da koda biyu, wani halitta ne kaman wake akwai wasu ma da suke da ɗaya jal kuma suke iya rayuwa amma kowa biyu Allah yayi mu da su, waennan kodar amfaninsu kuma su tace jininmu ne idan ruwa yayi yawa su cire ta ta hanyar fitsari, suna taimakawa wurin hana jini ya hau sannan suna kuma sake wasu kwayoyin halitta na hormones su hana ƙarancin jini suna kuma haɗa vitamin D dake ƙara karfin ƙashi. Akwai abubuwan da suke kashe koda ba sai ciwon sugar ba wani ma abu mai sauƙi kan iya janyoshi kaman rashin shan isashen ruwa, riƙe fitsari ki ga mutum yana jin fitsari ya matse shi sai lokacin da ya maka tukuna zaka tafi da gudu, yawaitar shan pain killers baya na ɗan ciwo a sha diclofenac, wani yatsa ma na ciwo ki ga an apka feldin yawaitar shan su akai akai to su suna zuwa ne su rufe jijiyar da yake kaiwa koda jini, a cikin jikin mu kuma koda na daga cikin organs da suka fi kowanne bukatar jini, Sai kuma hawan jini ya fi yawa ma a ƙasar mu yana taimakawa sossai wurin kashe koda waennan dalilan bayan ciwon sugar su kan iya haifar da ciwon ƙoda, a kan iya chanzawa a dace amma ni an chanza min duk biyu ba'a dace ba yanzu haka ina zuwa dialysis ko wani wata." Tamkar Afeefah za ta zubar da hawaye take juya maganganun Mammin "Mammi Allah ya baki lafiya ya sa kaffara ce duk kika yi ta yi" Mammi tayi murmushi tace "Ameen, kila Allah ya ajiyeni ne don ƙaddarar haɗuwarmu kila alkhairi zai haifar, bana fita kwata-kwata sai da Saraki ranar kawai na ji ina son fita ashe da rabon mu haɗu ne" Afeefah tace "Na ga Yaya..." Sai ta kasa cewa Rayyan a hankali tace "Ya Saraki! Ya damu sossai da rashin lafiyar naki" Mammi ta ɗan murmusa Allah ya sa kar Rayyan ya ji tana ce mishi Saraki don baya so, shiyasa ko su Abeeha ma Ya Rayyan su ke cewa "Afeefah ba zan iya misalta miki yadda hankalin Saraki ke tashi a kan ciwo na ba, ko kin san hatta me dafa min abinci ta karantu ne sossai akan cimar masu ciwon mu? Saraki ya tafi yayi courses akan likitanci ne bayan ciwon sugar na ya haifar min da wannan ciwon ƙodar in ba haka ba burin shi ya zama soja ne kawai ba Army medic ba, duk don ya san irin taimakon da zai bani a cikin gida ba sai mun yi ta zarya asibiti ba sanin bana so" Jinjina irin kaunar da yake mata take yi, lallai Rayyan na son mahaifiyarshi. Cigaba da mata hirar irin gudumawar da Rayyan yake bayarwa a rayuwarta take yi. A yadda dai ta gansu kaman babu wani namiji a gidan bayan Rayyan to mahaifinsu rasuwa yayi? Bata da wannan amsar sai dai ta san idan har tana gidan za ta sani ne. Abeeha ce ta shigo "'yan makaranta ashe an dawo?" Tayi maganan tana zama hannun kujerar da Afeefah take "Na dawo Adda Abeeha, makarantar akwai daaɗi they are all nice to me basu yi min dariya ba" "Ai na faɗa miki babu mai miki dariya, wasu da girman da suka fi naki ma suke zuwa suyi karatu bare ke da jikinki ba nuna girman yake yi sossai ba" "Aikam na gani kuma na ji daaɗi, ga malaman sun iya karantarwa komai fa fahimta nake kaman na sani tun da chan" Mammi da Abeeha suka murmusa, za ta sake magana kenan Ya shigo parlorn da sallamar da shi kaɗai yake sanin yayi kayanshi. Kai tsaye kusa da Mammi yaje ya zauna, da ita da Abeeha suka haɗa bakin ce mishi "Sannu da dawowa" Kai ya ɗan gyaɗa bai kalli kowaccensu ba, mammi ma ta mishi sannu da dawowa yake tambayarta ya jikinta ta amsa da da sauƙi. "Yauwa Mammi ɗazu na haɗu da Samha a school ashe auren ya salim wani sati?" Abeeha Tayi maganan da ɗan mamaki, Dukda da ta kalli Samha sai da ta tuna abubuwan da suka yi wa Afeefah kuma haushin su take ji har ranta ko da samhar tayi mata magana da kyar ta daure ta amsa, wurin kokarin janta da hira ne take sanar mata auren salim ɗin kuma suna gayyatarta. Wani irin faɗuwa gaban Afeefah yayi "Aure Ya Saleem zai yi?" Bata san a fili tayi maganan ba sai da ta ɗago idanunta suka faɗa cikin nashi da a lokacin ya ɗago ya kalleta jin furucinta, da sauri ta ɗauke ido gabanta na dokawa sam bata son suna haɗa ido bata san me yasa ba, sai dai yanzu maganar auren saleem ɗin sai ta ji shi wani iri duk ta ji babu daaɗi, Abeeha ma sai da tayi maganan kan ta tuna da Afeefar. Mammi ce tace "Eh aure zai yi Afeefah wani sati, kar ki wani sa damuwa a ranki in shaa Allahu Allah zai musanya miki da abin da ya fi alkhairi" Kunya ne ya rufe ta sai ta duƙar da kai tana kallon yatsun ta sautin tsakin shi ne ya shiga kunnenta, Mammi ta fara mishi faɗa akan yawan tsakin kaman wani tsaka, Abeeha ce ganin yanayinta ta ja Afeefar akan su je su ci abinci suka fice daga parlorn. **** Hidima fa ya kankama ɓangaren Amarya sai shiri ake wane, tun saura sati aka fara bikin 'yan karya don Mommy sossai ta ajiye musu kuɗi Dukda ma angon ya ja mata gargadi akan duk abin da za su yi kar su sake su saka shi, bai ma je gidan ba ko sau ɗaya sai ranar da suka yi kauyawa bayan Magrib yana zaune harabar gidan su da dangi suka cika, shiru kawai sam ba ya jin daaɗin komai kuma komai ba ya burgeshi kaman daga sama ya ji Muryar Mommy. "Saleem yanzu ka rantse sai ka nunawa duniya duka ba ka son auren nan dole na maka ko?". Shi bai san me yayi ba, kaman zai yi kuka yace "Me nayi kuma mommy?" "Ko sau daya ka je kofar gidan su Sabrina da sunan zance? Ko ita ba mutum ba ce? Ka hana ta saka ka cikin duk hidimar ta da kyar ma na bugi cikinta ta nuna min kai ne baka so ba ba bata sanar da kai bane, baka bata komai ba haka ake yi?" "Amma mommy ni nace tayi wani hidima ne?" "Au in kai kana ƙunci da baƙin hali a kan wata chan da na tabbatar yanzu ta rabarwa maza kanta sai aka ce ita ma ta biye ka kuyi ƙuncin tare?" Runtse ido yayi ya buɗe tuni suka sauya Meyasa mahaifiyarshi ke yin abu kaman bata je islamiyya bane? Ya subhallah maganar da ta faɗa ya mugun ƙona mishi rai amma ya zai yi ne? Uwa uwa ce. "Zan je, zan ba ta kuɗin" Abin da kawai ya iya faɗa kenan ba tare da ya kalli mahaifiyar tashi ba, sai da ta wuce ya bita da kallo yana jan Astagfirullah don yana tsoro, 'ya'ya mata ne garesu yana tsoron Allah ya hukunta mahaifiyar tasu da daya daga cikin yaranta, yana tsoro ta fahimci kuskurenta in a Hard way. A lokacin ya miƙe ya nufi mota kan ya shiga aka wangale Gate, motar Rayyan ne ya shigo cikin gidan dole ya fasa tafiyar sai ya nufi wurin Rayyan ɗin suka gaisa. "Fita za ka yi ne?" "Eh wai zan je ne in ba Sabrina kudaɗen da ya kamata su yi hidimar bikin" Kai Rayyan ya gyaɗa yana furta "zagayo mu tafi" Zagayawa yayi ya shiga motar, shiru yayi dama shi ne mai hirar muddin suna tare da Rayyan to shi ma baya cikin yanayin hiran, hakan kuma sai yake sa Rayyan ke jin wani iri sai ya ga kaman bai kyauta mishi ba ɓoye mishi da yayi Afeefah na gidan su amma zaman lafiyanshi kenan tunda mahaifiyarshi ba amincewa zata yi ba ko ya faɗa mishi ɗin. Har suka isa unguwar da saleem ne ke ta mishi kwatance hira ba sossai ya hada su ba, a cikin Layin aka yi kauyawan ana ta shirye-shiryen kiran sallahn isha su kam suna nan suna chasewa 'yan mata sai zuba rawa suke, Rayyan ya samu wuri yayi parking yana kallon arean da abin da suke yi a ranshi ya ja tsaki yayi dubu, auren saleem ne ake yi ake wannan haukan? Babu natsuwa a lamarin nasu babu kama kai, ba'a hana hidima ba amma sai a yi shi da tsari ba irin wannan ba ko daga rawar da ake ka san an zubar da mutunci. Wayanta ya shiga kira ringing na karshe ta ɗaga "Hello Ya Saleem" Ta faɗa da ɗan ƙarfi saboda kida dake tashi "Ki zo ina daga bayanku kaɗan" Babbar kawarta ta janyo jiki na tsuma suka nufi motar, baya suka bude suka shiga suna gaishe su. "Amma mun yi fushi sai yau abokanan ango ke neman mu?" Ci kan ku Rayyan bai ce ba, arzikin kallo ma basu samu ba yana wurin ne kawai saboda Saleem ne da wani ne waennan ɗin sun mishi kaɗan ya haɗa numfashi da su a mota guda. Bundles na 'yan dubu dubu guda uku ya buɗe dashboard ya fiddo ya ajiyewa saleem a kan kafafunshi dole ya ɗauka ya juya ya miƙa mata "Ku yi hidima." Jiki na rawa suka karɓa sai kamshi kudin ma ke fitarwa na sabunta. "Akwai wani abu?" Ya tambaya saboda kawai mommy ta mishi dole "A'a ya saleem wannan ma ya isa mun gode sossai" Daga nan suka fice don shi maganan soyayya ma ba wai hada su yake da ita ba. "Ka ga abin da mommy ta ja min ko Rayyan?" Saleem ya faɗa bayan sun fice daga unguwar. Hakika shima ya ga wautar mommy, da ya ga yarinyar sai ya hasko Afeefah a idanunshi ko a kusa bata da abin da za'a haɗa ta da Afeefah bai ce komai ba dai har ya mayar da saleem gida. Su Gaje sun yi shiri matuƙa na wannan aure, yayinda amarya tayi shagali sossai kuma ta kullaci kannen angon da babu wanda ta gani a hidimar ta har aka ɗaura aure ranar Juma'a, Dukda aure ne da babu wani sanarwa ko hidima saleem ya ga mutane kwarai an mishi kara, saboda shi ma na jama'a ne Rayyan na a gefenshi yana yi ne kuma saboda saleem ne don baya son harkar hidima da hayaniya har aka ci bikin aka watse, amarya dai ta tare a sashen saleem na gidan inda duk mommy ce ta tsara hakan sai fatan Allah ya basu zaman lafiya. 🖤Gureenjoh🖤 HAIHUWA DA HANJI (A True life story) Fatima Muhammad Gurin (Gureenjoh) Wattpad-Gureenjo6763 Arewabooks-Gureenjoh *FREE BOOK* *24* Da misalin ƙarfe ɗaya na dare ta jefar da mayafin kanta tare da dira daga saman gadon tana jan tsaki, me salim ke nufi ne? Babanta ya tabbatar mata shirin da aka yi akan shi ba mai sauƙi bane da zai iya resisting amma me ya faru har yanzu bai shigo ba? Ɗaukan maganin da Gaje ta bata a gefen bedside tayi ta jujjuya "To bai ma zo bama bare in sha wannan ɗin" ajiyewa tayi ta janyo wayanta kaman ta ƙira su Gajen kuma sai ta fasa ta nufi parlor, kasancewar sashen nashi ɗaki daya ne da parlor sai kitchen in har dai ya shigo to ba zai wuce yana parlorn ba sai dai idan a waje zai kwana. Shi kuwa salim tun karfe tara ya shigo gidan yanayinshi baya mishi daaɗi sam, fuskarshi babu walwala haka ya tura kofan da sallama ya shigo, yana taka door mat ɗin ya ji kanshi yayi wani diimmmmm jiri na shirin kwashe shi a hankali ya furta "Subhallah!" Ya tsaya a wurin sama da mintuna biyu kan ya sauƙe numfashi ya nufi three seater ya kwanta hannunshi dafe da goshinshi, duk yadda zai yi ya samu sauki ya yi sai dai wani irin tension yake ji, sai juye juye yake Sabrina da a chan ƙasan ranshi ya san bai damu da ita ba sai kai komo take yi a ranshi, bai san adadin lokacin da ya dauka ba shi ba mai bacci ba shi ba ido biyu ba, ko matse shi zaka yi ba zai ce maka ga abin da ke damunshi ba sai jin Fitowar ta yayi. Ganinshi ya sa ta nufe shi. "Ya salim dama ka shigo? Shine kayi kwanciyarka anan ina chan duk tsoro ya rufe ni?" Bai ce komai ba sai ido da ya ɗan zuba mata. "Ka tashi mu je ka kwanta a ciki idan baccin ne ma" Ta faɗa tana riƙo hannunshi, kasa mata musu yayi haka ya bi bayanta kaman rakumi da akala, a bakin gado ta ajiye shi ta shiga rage mishi kayakin jikinshi, wani sashi na zuciyarshi tsantsar mamaki yake na wannan bushewar idon wani sashen kuma na faɗa mishi ba laifi bane, har ta gama cire mishi kayan shi dai bai tanka ba kuma bai motsa ba, hannunshi ta ja wai tunda ba ya jin daaɗi su je ta mishi wankan, tana tura shi bayi ta dawo da baya ta sha wannan maganin da gaje ta bata don ta tabbatar mata yana kusantarta da maganin babu kuma wani abu da zai gane, babu wacce zai gani nan duniya bayan ita. Tun daga chan cikin bayin zancen ya sauya, ita ce ke jan ragamar komai kaman ba amarya ba har dai ta samu nasara a kanshi Dukda ita ce tayi kidinta kuma tayi rawanta abinda zuciya bata so gangar jiki ko an tilasta ta ba zata ba da abinda ake so ɗin ɗari bisa ɗari ba, shi dai ya san bayan nan bacci mai nauyi ya ɗauke shi tana kwance jikinshi tana zabga murmushin nasara. Washegari da kyar ya iya tashi yayi sallah a makare, yana zaune kan sallaya idanunshi na zube a kanta tana ta baccinta, duk ya rasa me yake tunani ko me yake ji kaman an yi blocking kwakwalwarshi da daidaitacciyar tunani, knocking da ake ta yi shi ya ɗaga shi daga wurin ya nufi kofan ya buɗe Samha ce. "Ina kwana yaya?" Kai ya gyaɗa bai ce komai ba. "Gashi in ji Mommy wai in kawo muku" Karɓa kawai yayi ya juya ya koma, ta tsaya tana kallon kofan for seconds kan ta tafi. Shirya abincin yayi kan ya nufi cikin ɗaki ya nufi bakin gadon ya shiga bubbuga hannunta. "Sabreena! Sabreena!!" "Uhmmmm" Ta faɗa cikin baccin tana haɗawa da tsaki "Wai menene?" "Kin yi sallah?" Ta sake jan tsaki kan ta buɗe idanu tare da Miƙewa zaune "Ka san gajiyar da nayi? Ai koyaushe na tashi zan yi Sallar yanzu ka tashe ni sai in yi ciwon kai ai" Da mita tayi maganar. "Ai in sallah bai tashe ki ba yunwa zai tashe ki, ga abinci chan ki fito mu karya" Yana kai nan ya miƙe ya fice yana ji kawai ya gamsu da something is off with him amma ba zai iya pointing menene ba. Sama da mintuna arba'in sai gata ta fito shirye cikin wasu riga da wando masu fadi, yana zaune yana jiran ta ganinta sai ya fara kokarin sanya musu abincin bata hana ba ya saka plate ɗaya zai saka wani ta riƙe hannunshi "Wannan ma ai zai ishe mu Ya salim mun riga mun zama ɗaya ai ko ba haka ba?" Kai ya gyaɗa yana zame hannun nashi ya ɗauki spoon ya saka, ita ta haɗa musu tea tana wani irin murmushi. Tun daga wannan rana saleem sai da ya kwana bakwai bai fita ko ina ba yana tare da ita, wani lokacin haka za su yini duk abinda tace zai gyaɗa kai kuma zai iya yi mata amma ba zai yi magana ba, itama kuma tana abunta da taku ne, ko sau ɗaya basu sauka sun gaida Mommyn ba suna gida ɗaya abinci kuwa safe rana dare daga wurin mommyn ake turo musu, wayanshi ma kashewa tayi kar ma a kira shi don dama ya ɗan samu hutun aiki. Yau mommy na zaune a parlor tana mamakin wannan sabon hali na Saleem kasa shiru tayi ta kalli Sadiqa tace "Yayanku kam duka cikin daaɗin auren ne za'a kwana bakwai muna gida ɗaya bai iya lekowa ya gaishe ni ba? Daga shi fa har Sabrinar tunda aka haura da ita ban ga keyarsu ba" Sadiqa tayi murmushi "Ai za ki musu uzuri Hajiya mommy kin san sabon shiga, amma na san dai duk yadda ake ciki yau kam kila su sauƙo kin san har da gajiya duka na hidima ya tarar musu" Samha dai bata gamsu ba amma ganin mommy bata sake cewa komai ba sai itama ta share. "Amma mommy ba kya tunanin akwai abin da yake damun Sameera? Yarinyar nan duk ta zama kaman ba ita ba don damuwa?" "Toh Sadiqa ya zanyi? Na yi tambayar duniya ta ce babu komai kila ku in kun saka ta gaba zata faɗa muku damuwarta" Sadiqa tace "Wlh ni dai ta ƙi faɗa min ban san ko Samha ba" "kawai karatu ne fah! Kin ga tana ta shirin shiga final year abin babu sauƙi" Ba wai sun yarda ba suka bar maganan, Sameeran ce ta fito ta zauna za tayi magana suka ji motsin takowa kaman ana saukowa daga stairs duk ido suka zubawa staircase ɗin sai ga Sabrina da Saleem suna jerowa idanunshi na kallon ƙasa yayin da take murmushi mai faɗi har tsakiyar parlorn suka zo bai ɗago ba, ganin zai fice mommy ta miƙe tsaye "Saleem" Waigowa yayi ganinsu ya ɗan shafa kai "Oh mommy ashe kuna nan, barka da safiya" Speechless ta zama ta kasa furta ko A, Sabrina ta kalleshi "Kayi sauri don Allah Ya Saleem idan ka dawo za'a yi gaisuwar" Ba musu ya juya ya fice, ta juyo tana murmushi ta zo ta samu kujera ta zauna "Mommy barka dai Fatan kina lafiya?" Ido kawai suka zuba mata, da kyar mommy ta kawo musu uzuri a ranta ta zauna tana cewa "Lafiya ƙalau ɗiyata ya zaman sabon wuri?" "Lafiya ƙalau mommy ai ba wani sabunta da yake duk gida ne kuma yayan yana kula da ni yadda ya dace" Kai mommy ta gyaɗa, samha da Sabrinar take sa'a da ita tace "kin tashi lafiya?" Murmushi tayi "Lafiya ƙalau ƙanwar mu" Harara ta maka mata Sabrinar tayi wani murmushi tana kallon su sadiqa tana jira su gaisheta. Mommy ce ta musu ido duk suka gaisheta ta amsa kuwa hankali kwance ita matar yayansu "Mommy kin ga ya fita yana sauri ko? Wlh Gaje ce bata ji daaɗi ba kuma Bakinta babu taste kwadayi take ji shine na ce ya je ya sayi kayan kwalam sai ya kai musu gidan ya kuma bata kudin magani" Mommy da kanta ya sake ɗaurewa tamau ta zubawa Sabrina ido sabon salo wai gada a kotu yaushe kuma aka fara hakan? "Ah yayi kyau" Abinda ta faɗa kenan, Sabrina ta miƙe "Bari na koma ciki" Tana kai nan ta haura saman ta Barsu da tunanin me ke faruwa? Sai dai babu wanda ya je da nisa saboda mommyn na mata uzuri kuma tana son ta da Saleem ɗin sai suka kama wani hirar daban. **** Yau sunday tun safe Afeefah ke tare da Mammi, hira suke yi kaman 'ya da uwa kafafun Mammin na kan cinyar Afeefah tana ɗan matsa mata take cewa "Mammi yau ƙafafunki sun kumbura dama yana miki haka?" "Yana yi Afeefah, ni kam me ba na gani ne? Yau kam ma na tashi jikin sai a hankali ai ni kaɗai na san me nake ji" Tayi maganan da 'yar haki tana kishingida. "Sannu! Ko zaki ƙara magani?" "Kayya bar zancen maganin nan Afeefah, je ki kira min Yayanku nayi ta gwada layinshi bana samu tun bayan asuba da ya shigo nan muka gaisa ban sake ganinshi ba" Idanu ta ɗan waro gabanta na faɗuwa, Dukda ta san ta inda Sashenshi yake amma bata taɓa gigin shiga ba to me zai kai ta? Yanzu ɗin ma jiki a sabule ta miƙe ta fice daga ɗakin, Abeeha bata nan tun safe taje gidan jiddah za ta raka ta asibiti wai bata jin daaɗi da ko ita zata iya zuwa amma ita har yanzu ganinta baƙuwa a gidan take, ko ba ma haka ba ina zata iya da wannan da ba'a mishi gwanintar? Mutum sai faɗin rai da masifa... Da kyar ta ɗaga hannu tayi knocking kofan parlorn sai dai shiru babu amsa, ta sake yin knocking karo na biyu nan ma shiru, a hankali ta tura kofar da sallama a Bakinta ta shiga yana kishindige very relaxed a cikin kujera, parlorn da hasken shi ba sosai chan chan ba sai tashin kamshi yake, kaman waya yake yi amma ba da wayar da ta saba ganinshi dashi ba gabanshi system ne shima a kunne kaman dai aiki yake yi ya tsaya amsa wayar. Daga ɗan nesa ta tsaya kanta a ƙasa tana jin yadda yake magana wane wani sarki, murmushi tayi a chan ƙasan ranta take raya dole Mammi ta kira shi Saraki don shi komai nashi ya fi yanayi da jinin sarauta, bayan ya gama wayan ya ɗan kalleta ba tare da ya ce komai ba ya ɗauke idanu itama jin shiru ya sa ta ɗago ganin ya gama wayan ta ɗan ƙara taku biyu sai ta rasa me za ta ce. Da kyar ta iya haɗa kalmar sunanshi akan lips ɗinta "Yaya Saraki..." Ɗagowa da yayi ya kalleta ya sa maganar datsewa, bai san ya ɗago ɗin ba don yadda ta kira sunan sossai ya dake shi, bayan Mammi bai yarda ya ji sunan bakin kowa ba amma jinshi a Bakinta sai ya rasa me yake ji ma, haushi ne ko takaici ko bacin rai? Tsam ya miƙe ya nufo ta. Idanu ta shiga zarewa takunshi na tafiya da bugun zuciyarta har ya matso dab da ita yace "Maimaita abin da kika ce?" Shiru tayi ta kasa magana idanunta da suka yi raurau alamun kuka ko wani lokaci ta ɗauke daga kanshi jikinta na tsuma ta ciki, kusan seconds huɗu kan ya ce "Allah ya so ki, da kin maimaita sai na fasa miki baki ke Mammi ce da za ki kira ni Saraki? Wani Yaya Saraki...!" Ya sake maimaitawa yana ɗan harararta. "Me?" Ya faɗa yana dan gyara tsayuwa idanunshi tsamm a tsaye a kanta ko a jikinshi. "Yaya..." Wlh sai ta kasa cewa Rayyan ɗin tayi tsai tsammm sai ma ta fasa kiran sunan da ɗan saurin baki tace "Mammi ce wai ka je!" Ta juya za ta fice yace "Tsaya!" "Ba ni da suna ne? Ko da gini kike magana?" "Innalillahi wainna ilaihi rajiun..." Ta faɗa kaman za tayi kuka chan ƙasa, sarai ya ji ta "Ga musiba tsaye gabanki ko?" Girgiza kai tayi, tsaki ya ja yace "Bar nan" Da sauri ta fice. Sai da ta ganta tsakiyar babban parlor kan ta dafe kirjinta tana sauƙe numfashi, Rayyan na son kasheta da ranta, yaushe ya iya ma dogon magana haka bata sani ba, shi da komai ko oho ne me yasa zai saka ta a gaba yayi ta razana ta! Jiki a sabule ta ƙarasa wurin Mammi "Wai yana zuwa" Zama tayi kawai bata sake cewa komai ba, mintuna basu wuci uku ba sai gashi gaban Mammin kawai ya ƙarasa ya fara taɓa temperature ɗinta, numfashinta baya fita yadda ya kamata hankalinshi tashi yayi, a take yace su tafi asibiti duk yadda Mammin za ta ƙi ya nace ya dubi Afeefah yace ta ɗauko mata mayafi, da sauri taje ta ɗauko duk sai ta shiga damuwa ganin yadda hankalinshi ya tashi, kuma dai a fili Mammin bata yi tsananin da ya kamata ya ɗaga hankalin nashi haka ba, bata zauna ba itama gyalen da ta ɗaura a kanta na Jersey ta warware ta yafa akan doguwar rigar atamphar dake jikinta ta bi bayansu, a gaba ya saka mammin ta buɗe baya ta shiga suka fice daga gidan. Tafiyar mintuna ashirin ya kai su asibitin shi ya sake kama mammin suka yi inda za'a duba ta don ya riga yayi call, tuni suka karɓeta don a yi mata gwaje gwaje a tabbatar da babu abin da ya sake tsananta ko chanzawa. A reception ta zauna idanunta na kan yatsun ta sai adu'ar samun lafiya take yiwa Mammi mata mai kirki da mutunci, macen da ta zame mata uwa kuma garkuwa a yanzu. "Afeefah...!" Da ɗan karfi ta ji an kira sunanta har bata san ta ɗago a razane ba sai... 🖤Gureenjoh🖤 HAIHUWA DA HANJI (A True life story) Fatima Muhammad Gurin (Gureenjoh) Wattpad-Gureenjo6763 Arewabooks-Gureenjoh *FREE BOOK* *25* Sulaiman kaman zai kama hannunta haka ya tsaya gabanta yana kallonta. "Da gaske ke ce? Ashe zan sake ganinki Afeefah? Ina kika shiga? Kin san irin neman da na miki?" Idanunta na sauƙa kanshi ta miƙe tsaye, ganin irin kusancin su ya sa ta ɗan yi taku biyu baya fuskarta a sake tace "Ina nan Dr. Allah ya haɗa ni da mutanen kirki" "Afeefah me yasa ba ki zo office na ba? Me yasa ba ki neme ni ba da mahaifiyar saleem ta kore ki?" Idanunta ne suka cika taf da kwallah a hankali tace "Ban san inda zan sameka bane ban san sunan asibitin ku ba ko in ce ban riƙe ba, ko ma na riƙe ba ni da ko biyar da zan hau abin hawa in ce a kawo ni" Idanu ya ɗan runtse kaɗan ya buɗe da sauri sai ya ga kaman za ta iya ɓace mishi any moment "Ina kika shiga to? Waye ya taimake ki?" "Na haɗu da mutanen kirki sun tallafeni daidai lokacin da na buƙata kuma suna riƙe ni tamkar ɗaya daga cikinsu yanzu haka ina makaranta" "Alhamdulillah!" Zama yayi saboda a lokaci ɗaya daaɗi da baƙin ciki duk suka haɗu mishi, itama ta zauna a hankali ya ce "Afeefah har Dutsen-wai na je nemanki" Da sauri ta ɗago ido suka haɗa idanu ya gyaɗa mata kai alamun tabbaci. "Gidan kawu ka je?" Kai ya gyaɗa cikin nuna damuwa ya ce "Abin da muka tarar ba karamin tsoro ya bamu ba Afeefah, ban so ba, ban san hakan zai kasance ba da ban yi ganganci da kuskuren tafiya da manya na ba" A lokaci daya ta zama very confused sun je gidan kawu? Me suka tarar? Me yasa yaje da wasu?. "ko da ban furta miki ba kin dai san Sonki nake ko Afeefah?" Lumshe ido tayi kalamar na sauka mata wani iri a zuciya. "A lokacin da na samu labarin tafiyar ki i was very disturbed na ɗauka chan gida za ki koma, ko da na koma gida na samu mahaifiyata da labarin ban gama bata ba Abba ya shigo ya ji zancen, dama ya matsu kuma da maganan aurena dole ya haɗa ni da Yayyenshi kuma ya kafa hujja ne da cewa a musulunce ma bai halatta namiji ya fara taran mace ba tare da sanin iyayenta ba.. Dole ta sa muka tafi tare da su ba don na so ba" Hawaye ne ya zubo mata a kan fuska ta ɗan yi murmushi mai yanayi da wani ciwo a ƙasan rai ta ce "Sun ji kunya ko? Na tabbatar ba su amince maka ba kuma ba za su taɓa amince maka ba..! Ka yi haƙuri, da na san za ka aikata hakan da ni da kaina na faɗa maka wacece ni kafin ma ka je" Ya ɗan haɗiye wani abu mai ciwo a hankali yace "Afeefah sun yanke min hukunci mai girma a yanzu haka ina da aure, an ɗaura min aure last week saturday amma har yanzu zuciyata ke take so, ke take marararin rayuwa da ba wata ba. Na haƙura na karɓi auren ne saboda ban san inda zan ganki ba ban san inda zan sameki ba, a ina ne gidan da kika koma? Idan kin ga da takura za ki iya dawowa wurin Umma na tabbatar ita me riƙe ki ce tamkar ɗiyar da zata haifa a cikinta" Rayyan ne ya fito sai idanunshi ya faɗa kan su, a kan hawayen dake bin ƙuncin ta ya ɗan tsayar da idanun kan ya ɗauke kai ya zo ya wuce su kaman bai gane su waye ba, Afeefah da suka haɗa ido ta sa hannu ta share hawayen fuskarta ta dubi Sulaiman "Zan tambayi Mammi zan zo in gaishe Da Umma! Amma batun soyayya don Allah ka ajiye shi a gefe Dr. Kai fa ka gayamin irin abubuwan da Kawu ya muku na ba da kunya, taya za ka yi convincing iyayenka su sake komawa irin gidan chan?" "Zan iya Afeefah kawai ki ba ni dama!" Ta girgiza kai "Aurenka fa?" Zai yi magana ta ce "Ka yi haƙuri Dr. Yanzu ba lokacin wannan maganan bane marar lafiya muka kawo" Shigowar Abeeha da Jannah ne ya sa ta ƙarasa share fuskarta ta ƙirƙiro murmushi ta saka, suka ƙaraso kusa da ita "Afeefah ya jikin Mammin?" Ta ce "Da sauƙi sossai amma tunda Ya Saraki ya shiga da ita ba'a fito da ita ba" "Amma Yaya Rayyan ɗin yanzu muka wuce shi a waje yana waya" "Eh shi kadai ne ya fito" Gaisawa suka yi da Dr. Sulaiman yana mamakin jin ana ambaton Rayyan, gidan su Rayyan ta koma? "Afeefah ko zan iya samun Layin da zan yi magana da ke?" Ya faɗa yana kallonta, kallonta Abeeha tayi sai ta ɗan yi murmushi tace mata "Dr. Sulaiman kenan!" Shima ta juya tace "Yayyena ne Addah jannah da Adda Abeeha" Murmushi yayi lallai Afeefah ta samu wurin zama idan har ta sake da ahalin haka sun zama tamkar jininta ya tabbata ba zata iya barin su ta dawo wurin ummanshi ba yadda ya ci buri. "Dr bamu natsu ba har yau bamu samu mun je mun sayi waya ba, bari na baka layina za ku iya dinga gaisawa kan ta samu nata" Godiya sossai yayiwa Abeehar, ta bashi contact ɗinta ya tafi da sauri ta juyi wurin Afeefah tana murmushi sai ta ga damuwa a kan fuskarta, dafa kafaɗarta tayi "Ya dai?" "Adda wai Shima aure yayi last week saturday" Duk sun ji maganar wani iri amma sai suka dinga nuna mata babu komai kila ba rabonta bane ko kuma Allah ya kaddara za ta zama matarshi ta biyu bata san ta cewa Abeeha ba "A yaushe kenan? Aure last week Adda Abeeha kina tunanin ko shekara daya ne zata amince ya mata kishiya a kusa haka?" "Duk ba mu san tsarin Allah ba, mu yi Adu'a kawai duk abinda ya kaddara daidai ne" Ta gamsu amma har lokacin ranta na suya da abinda kawu ya aikata, kenan akwai ɗan sunnar da zai aureta a duniya kenan? Waye zai yarda ɗan shi ya auri irin ta matukar za su bincika asali da tushenta? Bata san Rayyan ya dawo ya wuce ba chan sai ga shi sun fito da Mammi, duk Miƙewa suka yi suna mata sannu tayi murmushi "Duk rigimar Saraki ne amma jikin nan bai kai zuwa Asibiti ba, Jannah ya jikin naki?" "Da sauƙi Mammi, sannu Allah ya baki lafiya" Ta gyaɗa kai. Idanunta ta kai kan Afeefah dake ta murmushin yake "Afeefah kina lafiya? Na ga damuwa a fuskarki" "Babu komai Mammi sannu da jiki" Kai ta gyaɗa ba wai don ta yarda ba suka nufi mota, ƙin shiga motar Rayyan tayi don wlh tsoron ko motsi take a gabanshi, motar Jannah ta tafi suka haɗu su uku suna hirarsu har gida. A babban parlor suka yi masauki don Rayyan ya riga su isa kuma ya shigar da Mammi ciki ko da ya fito a babban parlorn ya tsaya yana nuna su da yatsa "Ba ku parrots ba? To in ga watan ku ta shiga ciki tana damunta da surutu ko wata taje tana saka ta gaba da kukan banza ku ga abin da zai faru" Yana kai nan ya wuce abin shi basu motsa ba sai da ya ɓace Abeeha da Jannah suka tafa suna sheke wa da dariya, Afeefah na murmushi. "Mutum yayi ta muzurai kaman a filin daga yake" Jannah ta faɗa, Abeeha tace "Ai ke baki ganin komai tunda yanzu kin bar gidan nan da sauƙin ki" Jannah ta girgiza kai "Kema kin san babu wani sauƙi wlh sai dai in ban yi wani abin ba Ya Rayyan bai game shi ba ya je har gidan auren nawa ya zane ni tsaff" Ita dai Afeefah bata ce komai ba idanunshi kawai take gani, a hankali ta ɗan yi murmushi tana girgiza kai. Jannah bata tafi ba sai dare, sun sha hira sun ci sun sha, kuma sai da suka cika Mammin da surutu don yana fita daga gidan suka yi ɗakin suna bata labarin gargadinshi tana dariya ta dubi Afeefah "Afeefah ke ce me kukan banza kenan? Me aka yi miki za ki zo ki min kukan?" "Ba ayi komai ba fa Mammi" "Afeefah ki faɗa min damuwarki wlh ina hangar damuwa a tattare da ke" Kanta ta duƙar Mammi ita uwa ce, uwar ma ta wannan baudadden mutum ai dole ta san expression na kowa. Abeeha tace "Mammi Dr. Sulaiman yayi aure shima ashe" Mammi ta kalli Abeeha kan ta kalli Afeefah tace "Auren ne ya dame ki ɗiyata? Kin ga fa duk abin da Allah ya hanaka ba rabonka bane wanda kika ga kin samu shi ne rabon ki, in shaa Allahu za ki samu miji na nunawa sa'a" A hankali tace "Mammi ba auren shi bane damuwata" "Toh menene Afeefah?" "Mammi bana tunanin zan auru, Musulunci ya yarda a auri mace don kyaunta, dukiyarta ko nasabarta, sannan bincike a aure kaman dole ne a musulunci akwai dangi na ƙwarai da za su je bincike a kaina su yarda su bar ɗan su ya aureni? Mammi kin ji abinda su Sulaiman suka samu kawu suna yi a kan layi? Kin ji abinda aka fada musu a kaina daga shigar su kauyenmu?" Hawaye ne ya tsinke mata ta fashe da kuka tana jin ciwon Taɓon ta da bata tunani har Abada zai gogu. Jannah da Abeeha har sun fara tayata hawaye don idan ka ji yadda take maganan za ka san abin na mata ciwo kwarai da gaske.. "Afeefah zo nan" Mammi ta ƙirata, Miƙewa tayi ta isa kusa da ita Mammin ta ɗora ta akan kafaɗarta tana shafa mata kai. "in shaa Allahu Afeefah sai kin auri mijin da kowa sai ya ji sha'awar kasancewa ke, nagartaccen namiji kuma mai tarin ilimi da baiwa na musamman, kawunki ko mutanen garinku ba su isa sun shafe abin da Allah ya rubuta ba, ko kin manta Allah da kanshi ya faɗa mana yana fitar da mummuna cikin kyakyawa ya kuma fitar da kyakyawa cikin mummuna? Ba fa a suffa ko sura ake magana ba ana magana ne akan hali da ɗabi'a. To ki sa a ranki mijin da Allah ya zaɓa miki yana nan kuma idan lokaci yayi za ki aure shi ba makawa kar ki wani damu kanki kin ji?" Kai ta gyaɗa cike da gamsuwa "Na gode Mammi" "na ƙara ji sai na Buge bakin godiyar" Murmushi duk suka yi don da wasa tayi maganan. ***** Hajiya Hussaina tun fa tana tunanin abin na Saleem da Sabrina wasa ne har ta fahimci da gaske ne, domin yau tana zaune a parlor Sabreenar ta sauƙo ta ɗan kalleta tace "Sannu Mommy" Bata jira ta amsa ba ta wuce kitchen ta samu Talatuwa na aiki, ta ce "Talatuwa me kike dafawa?" "Tuwo ne da miyar egusi shi mutanen gidan suka ce a dafa musu" "Toh bari ki ɗora min fried Rice da kaji iyayena za su zo ganin ɗakina ba zan tarbesu da tuwo ba" "Amma S..." "Kin yi abinda nace ko sai na bi ta kanki? Har kin isa ja da ni typical 'yar aiki? Toh wallahi ki kiyaye ni" Sadiqa da ke shigowa ne tace "Haaa me ke faruwa da ihu haka?" Talatuwa ce ta mata bayani sadiqa ta kalleta sama da kasa "Amma ba ki da hankali yanzu su Gajen ne baƙi da har za'a dafa musu kaza da wani fried Rice? Dama shi suka saba ci a gida?" Sabreena ta riƙe baki tana kallonta na seconds kan tayi wani murmushi kawai ta juya fuuuuu ta fice. Mommy na nan zaune tana tunanin wannan lamarin da bata gane kanshi ba bare ƙasan shi ta ga wucewarta kamar iska, ba'a fi mintuna biyu ba sai Ga saleem rike da belt nashi na sojoji ko mommy bai kalla ba ya shiga kicin ya ya kuwa samu Sadiqa ya rufeta da dukar kawo wuka.... 🖤Gureenjoh🖤 HAIHUWA DA HANJI (A True life story) Fatima Muhammad Gurin (Gureenjoh) Wattpad-Gureenjo6763 Arewabooks-Gureenjoh *FREE BOOK* *Ku lallaɓa wannan kaina ciwo wallahi kaman zai faɗi* *26* Ihu take yi sossai na neman agaji, shi kuwa tamkar wanda ake zuga shi dukan ta yake kaman an aiko shi cike da wani haushi nasu da dama yana kwance ƙasan ranshi, Mommy da ta shigo da gudu ne ta riƙe belt ɗin a tsorace take cewa "SALEEM! SALEEM!! Me haka? Me ya hau kanka? Sadiqa fa kake yi wa wannan duka kaman wanda ya kama ɓarawo? Sadiqa fa ba sameerah ko Samha ba?" "Na kula rainin sun ya fara yawa ne, kuma wallahi kaɗan na mata ko kallon banza ta sake yiwa Sabrina ta gani bare zagin iyayenta sai na yi ƙasa ƙasa da ita, marasa kunyar yara kawai..." Yana kai nan ya wuce fuuuuu mommy dake tsaye kaman an dasa ta jiri ya kwashe ta ta tafi zaune. "Innalillahi wainna ilaihi rajiun me ke faruwa?" Sadiqa da baƙin ciki kaman ya kasheta tana dukunkune gefe tana kuka sossai don ba laifi ta bugu ta ce "Me kuwa mommy? Duk wa ya ja mana? Wlh babbar alamar tambaya ne akan yarinyar nan dama ni ba sonta nake ba kika saka shi dole aurenta yanzu wa gari ya waya? Tun fa ba'a je ko ina ba mommy wlh ba zan iya zama da yaya a wannan gida ba, ni zai daka? Akan Sabreena da take ƙanwar ƙanwar bayana?" Samha ta je ta kama sadiqa a tsorace take don jikinta duk rawa yake, ita dai Sameera bata ce komai ba ta juya ta fice, zuciyarta rawa yake kuma a cunkushe yake tana ji Mommy na fashewa da kuka tana tambayar me ke faruwa ita ta kasa gane komai me ya hau kan ɗan ta? Ko ci kanku bata ce ba. Samha ce ta taimakawa sadiqa da ruwan zafi yayinda ta dawo parlor wurin Mommy ta zauna suka yi shiruuu ita mommy tana tunanin me ya kamata tayi? Me yake faruwa ita bata gane komai ba, Sabrina ta sauƙo tana waka ta wuce su zuwa kitchen ta tabbatar Talatuwa ta ɗora mata abinda tace kan ta dawo ta haura ko kallon su mommyn bata yi ba. "Ashe yarinyar nan macijin sari ka noke ce?" Mommyn ta faɗa cikin mamakin duniya da ya rufe ta. Ina hijaban? Ina ladabin? "Mommy me ta yiwa yaya saleem? Ki dubeshi a kwanakin nan kaman ba shi ba duk ya zama wani iri ga faɗa da masifa ga saurin duka mu da tun muna kanana ma bai dake mu ba sai yanzu?" Samha ce me maganan zuciyarta har lokacin yana bugawa "Nima na kasa ganewa Samha kaina ya kulle tamau, kwakwalwana ba ya tunani daidai... Amma bari iyayen nata su zo mu ji me kenan?" A parlorn suka cigaba da zama chan kuwa sai ga Gaje da Yaya sun shigo, yanayin shigar tasu ma ba yadda suka saba zuwa ba a raɓe a raɓe a baya suna tsoro kar su yi ma mommyn ba daidai ba, kai tsaye suka zauna cikin kujerun parlorn yaya yana cewa "Hajiya Hussaina ashe ana nan, barka da gida" "Sannunku da zuwa" Ta faɗa tana ta kallonsu kaman sabbin halitta yadda suka shige cikin kujera duk ba haka suke yi a baya ba, bata gama mamaki ba sai da Sabreena ta zo da gudu ta rungume Gaje tana musu oyoyo "Masha Allah, Amarya kin sha kyau da kamshi" "kai Gaje, Baba sannu da zuwa" Ta faɗa tana daga jikin Gaje dake ta riritata. "Barka dai 'yar arziki irin albarka, ya sabon wuri? Babu takura ko?" "Ah baba wa ya isa ya takura ni ni da gidan mijina" Suka yi dariya. "Yana zuwa ya gaishe ku, sa kaya yake yi" "Ah ba komai ai muna nan" Mommy tana zaune tayi tsamo tsamo kaman ruwa ya daki babban zakara har Saleem ya sauko ya zo ya tsuguna suka gaisa da su Gaje sai albarka suke sa mishi kan ya miƙe ya kalli Sabreena yace "Na fita" Da sauri ta miƙe ta bishi muryarta na fita a lokacin da take cewa ka zo min da... Sai dai bata ƙarasa da karfi ba, bayan ya fita ta dawo ta saka su Gaje gaba banza suka yi da su Mommy kaman Allah bai halicce su a wurin ba, wasu irin hawaye ne ke zubowa Sameera tana ambaton sunan Allah kan ta tashi ta shige ɗaki tana fashewa da kuka. Samha dai da mommy sun kasa magana, suna kallo har ta musu iso dining suka ci suka yi nak suka dawo parlorn, mommy ta kasa shiru tace "Yaya...!" Kallonta yayi "Menene yake faruwa ne? Na rasa gane kan Sabrina tunda aka yi auren nan, ɗazu fa har sa wa tayi Salim ya daki sadiqa abin da ba halinshi ba, ba haka na saka shi ya aureta su zauna ba ba zan zuba idanu mu cigaba da tafiya a haka ba, Salim ko kallon mutunci ya daina min daga aure? Me hakan ke nufi?" "Hajiya Hussaina ke fa kike ɗaukar abu da zafi, yaro yayi sabon aure ai ba za'a saka musu ido ba, tarbiya daidai gwargwado mun ba Sabrina kuma idan Sadiqa tana mata gani gani da a matsayin ta na yayarta yanzu yayansu take aure ya kamata su san maganan da za su dinga faɗa mata ina ga hakan sai a zauna lafiya" Mommy ta saki baki da hanci tana kallonsu. Sabrina tayi murmushi tace "Abin da mommy ta kasa ganewa kenan, mu ajiye batun nan ku tashi mu je ku kalli sashena" Basu bi ta kan 'mommy ba suka bi bayan Sabrina, numfashi ne taji bata iya ja da kyau Samha ta riƙe hannunta "Mommy...! Mommyyyy!!" Hankali tashe take kiranta kiran ya fito da Sadiqa da Sameera ruwa suka dauka suna shafa mata a fuska har ta Fara sauƙe numfashi da ƙarfi, me su Yaya suka yiwa yaronta? Sai yanzu tunanin za su iya cutar mata dashi ya zo mata innalillahi kawai take ta maimaitawa a tsananin tsorace. Su kam suna hawa Sabrina tace "kun yi min komai iyayena, ba ni da abinda zan saka muku kun ba ni wannan daula da dukiyar sai yadda naga dama zan juya shi, a yanzu ma ina ragarwa uwar ne saboda wani dalili nawa amma itama nan kusa za ta gane ta ɗauki goruba ne ta damkawa kuturuwa don kwace saleem a hannuna sai mutuwa" Dariya suka sheke dashi Gaje tace "Ke gidan nan fa duk na mijin ki ne kina da ikon yin yadda kike so, sai na ga kaman wannan sashe yayi muku kadan kenan ku suka raɓa ba ku kuka raɓa su ba" Hakane kuma gaskiya Gaje, kai Sabrina ta gyaɗa "Zan san abin da zan yi akai, amma ko za ku dawo nan ɗin ne?" "Ta ya kenan 'yar albarka?" Baba ya faɗa, ta saki murmushi "Kar ku damu na san yadda zan yi saleem yayi musu korar kare a gidan nan" Hira suka cigaba da yi wane sa'anninta ba iyayenta ba duk wani tuggu sun haɗa shi a ƙarshe baban ke cewa "Ai duk yadda za mu yi mu yagi rabon mu kan a je lahira za mu yi, ko a gaban Allah laifin mu kadan ne ita ta ga dama ta bamu hanya zuwa cikin gidanta shekara nawa ina faɗi tashi akan ya kula ki sai da na hakura na cire rai kwatsam ta dawo da zancen ashe muna da rabon dangwalar arziki mu ma, bari mu je mu fara tattare" Sallama suka mata suka bar gidan ransu kal... **** "Saleem..." Ya kira sunan yana zama gangar shi, buɗe rinannun idanunshi yayi ya zuba su kan Rayyan ɗin ba tare da ya ce komai ba, duk wannan ɗin ba halin Saleem bane na Rayyan ne hakan ya sa Rayyan ɗin ya ɗan damu. Yana zaune kawai ya ga Shigowar saleem ɗin office ɗin kuma bai ce mishi komai ba bayan sallama ya samu wuri ya kishingida. "Menene? Me yake damunka?" "Ni ma ban sani ba Rayyan, kawai ina jin ƙunci ne raina babu daaɗi zuciyata na mini zafi ba na iya bacci" "Saleem kana karatun Alqur'ani?" Ya girgiza kai don ya fi 2weeks rabon da yayi karatu in ba a sallah ba. "Alqur'ani wani dafa'i ne na yaye ƙuncin zuciya saleem, idan ka ga ba zaka iya bacci ba kayi ta nafilfili kana karatun za ka ji sauƙi, ka fi kowa sani na har a yanzu bana bacci kaman na mutane amma da na riƙe ibada ban zauce ba... Ka roƙi Allah ya yaye maka dukkanin damuwowinka" Kai ya gyaɗa, Rayyan bai kara cewa komai ba ya tashi yayi playing karatu a office ɗin ya je ya ɗauko ruwa ya kawo mishi ya ɗan sha tare da kwanciya a three seater abin mamaki tun karatun na shigar shi har bacci mai tsananin daaɗi da natsuwa ya ɗauke shi ba tare ma da ya san yayin ba. Saleem ya yi baccin Awa biyu cip kan ya farka har lokacin Rayyan na office ɗin yana wani aiki a system ganin ya farka ne ya mishi sannu, kai ya gyaɗa ya miƙe ya shige toilet da ke ta tashin kamshi wanke fuska yayi tare da alwala don ana ta kiran la'asar, bayan ya fito Rayyan ma ya rufe duk abin da yake yi don baya tunanin daga masallaci zai dawo office ɗin ya shiga bayin yayi alwala ya fito yana gyara hannun lafiyayyar farar shirt ɗin shi da ya ɗora akan navy blue wandon jeans, rigar suite ɗin ya dauka da briefcase ɗinshi suka fice yana kulle office ɗin. Sai da ya zube abubuwan a mota suka isa masallaci suka yi sallah. "Za ka iya driving ɗin ko in mayar da kai" "No zan iya" Ya faɗa a hankali. Da kallo ya bishi har ya shiga motar shi ya bar wurin, ƙasa natsuwa yayi da yanayin saleem ɗin duk sai ya tsaya mishi, da wannan 'yar damuwar ya nufi gida horn yake dannawa a kofar gidan da gudu aka wangale mishi gate ya cusa motar ciki, idanunshi ne suka faɗa kanta sanye take da wani stylish crepe Adire ta haɗa shi da matching colour purple na Jersey, daga inda yake yana hangar labbanta dake shekin man baki sossai tayi kyau amma shi ba kyaun yake gani ba. Dr. Sulaiman dake tsaye yana mata magana ya ɗan zubawa idanu kan ya ƙarasa parking ɗin ya sauƙa sai ya ɗauke kai kaman bai san akwai halittu wurin ba, tafiya yake kaman ba zai taka ƙasa ba har ya ɗan gota su Dr. Sulaiman ya taso "Assalamu Alaikum warahmatullah Dr. Rayyan" Sai da ya ɗan lumshe ido ya buɗe kan ya ɗan waigo ya kalleshi ba don ya san muhimmancin sallama ba babu abinda zai sa ya amsa, hannu ya miƙa mishi suka gaisa ya juya ya shige ciki fuskar nan kaman an mishi mutuwa. Sai da ya ɓace ta sauke numfashin da ta riƙe Dukda ko kallon inda take bai yi ba, kwarjinin shi ya matuƙar cika ta ta tabbatar haka Sulaiman ma don babu wanda baya shan jinin jikinshi a duk sadda Rayyan ya matuƙar tsumewa, ita dai ta san Rayyan ba ya rasa nasaba da sarauta. "Afeefah me kika ce?" Dr. Sulaiman ya faɗa "Zan tambayi Mammi in shaa Allah in ta amince tunda gobe half day juma'a sai ka zo mu je in na tashi school" "Toh shikenan, ga wannan" Ya miƙa mata leda kin karɓa tayi sai da ta ga ranshi ya ɓaci kan ta amsa don bata yadda ta iya. Kai tsaye wurin Mammi tayi don ta bata ledar ba ma ta bukatar buɗewa kan ta kai mata, da kuwa ta san abinda zata tarar da bata shiga ba faɗa sossai Rayyan ke yi na shi baya son tarukuce idan abinda zata yi kenan ta tattara ta bi samarin nata yaushe har ta tafasa da zata ƙone? Haka ta ga Abeeha na yi? Toh shi ba irin tarbiyar da yake ba ƙannenshi ba kenan in kuma tana gidan dole tayi abinda ta ga su Abeeha na yi. Jikinta rawa ya ɗauka, Mammi ta riƙo hannunshi "Duk faɗar nan na Sulaiman ya zo ba tare da ka sani bane? Kayi hakuri ni ce na mata izinin fita ba haka kawai tayi fitan gaba gadi ba kuma ko mintuna biyar bai kai ba idan nima na yi laifi sai in ji..." Shiru yayi bai ce komai ba. Tana tsaye a gefe kaman yajin kosai kafafunta kaman za su kayar da ita saboda yadda suke rawa don mugun kallon da ya aika mata, ledan hannunta ya kalla "Ba kin ga kalar rainin da bana so ba Mammi? Mun ce ba mu dashi ne da zai kunso koma menene a leda ya kawo mata? Ko ta tambayi abu ba'a yi mata ba?" "Saraki...! Bana so! ka ga bana so don Allah, ka duba yadda ka firgita ta? In kuma hankalina kake so ka ɗaga ka cigaba" Da ɗan faɗa tayi maganan, haushin kanshi ya ji ina ma ruwan shi da zai damu da tarbiyar ta? Shi ba wani tsiyar yake dubawa ba sai kar ta lalace da tara samari tun bata kai lokacin ba, Miƙewa yayi ya nufi fita daga ɗakin ranshi a haɗe fuskar nan murtuk, wani irin chill abu ne ke bin jikinta na tsoro, bata san me yasa shi baya wani damuwa da damuwarta ba a ranta take jin kaman bai yi na'am da zamanta a gidan nasu ba, ita idan ba don mammi ba wlh ko inuwa ba zata so haɗawa da shi ba bare har magana, gashi nan tana ta aikata laifin da zai ji haushinta. Kamshinshi ne ya daketa a sadda ya wuce ba tare da ya ko kalleta ba ta lumshe ido sai da ta tabbatar ya tafi ta sauke numfashi ta isa wurin Mammi tana jin hawaye na tsinke mata "Mammi ki yi haƙuri ban san ba'a haka anan ba, na fita ne ba don wani abu ba sai don Roƙon da Dr yayi ta min a kan ko ba zan ɗauke shi Masoyi ba in ɗauke shi wa da zan iya neman abu a wurinshi yayi min, ya ce min Mamanshi ta damu tana so in je ta ganni ta ji lafiya ta don kaman 'ya itama ta ɗauke ni wlh ba ni na roƙe shi ba Mammi kin ga da kyar na karɓa har saida ranshi ya ɓaci..." Dafa ta Mammi tayi "Natsu Afeefah! Ki natsu kar masifar Saraki ya dame ki, haka yake wlh kin ga su jidda basu isa su kula saurayi ba sai ya fara zuwa ya ganshi yayi bincike ya amince mishi kan ya zo idan yayi bincike bai mishi ba ko wayanshi suka sake ɗauka mai karbar su a gidan nan sai ya shirya, na sani a yanzu babu zancen aure tsakanin ki da Sulaiman shiyasa na bari kika fita, kuma ai ba'a mayar da hannun kyauta baya... Goben ki shirya sai ku tafi da Abeeha in ta dawo school ku gaishe da mahaifiyar tashi kinji?" Tsoro ne ya sake rufe ta jin yana duka, itama kenan zai iya bugun ta in tayi ba daidai ba "A'a Mammi ba sai na je ba, zan bashi uzuri..." "Kar ki wani damu zan mishi magana" Ledar ta ajiye don ji take ko abin ciki bata sha'awar gani, hankalinta ba'a kwance ba ta tashi tayi ɗakinta ko da ta shiga sai da ta sakawa kofar key don ji take kaman zai biyo ta ya cigaba da faɗa. 🖤Gureenjoh🖤 HAIHUWA DA HANJI (A True life story) Fatima Muhammad Gurin (Gureenjoh) Wattpad-Gureenjo6763 Arewabooks-Gureenjoh *FREE BOOK* *FATIMA A MUHAMMAD Sirikata kuma namecyna ina so in yi amfani da wannan dama in miƙa saƙon godiya da kuma jinjina bisa irin kokarin da kike yi a kan wannan littafi, haƙiƙa ba ni ma da kalmar da zan nuna miki jin daaɗi na da kuma yabawa mai tarin yawa wannan shafin naki ne kiyi yadda kika ga dama da shi... Jama'ar gidan haihuwa da hanji conversation room ina ganin tarin comments naku sai dai lokaci baya bani dama a kullum na shiga a sha fira da ni amma ina matukar jin daaɗi kuma ina yabawa ku sani muddin Aminiyar ango(Fatima A Muhammad) ta amsa wallahi kaman ni ce nan na amsa. Ina kuma yi muku albishir gobe public holiday za mu samu damar jero shafuka biyu in Allah ya yardar mana. Na gode sossai* *27* Washegari friday har ta je school ta dawo bata daina tuna irin faɗar shi na jiya ba, ita kam ba don mammi ta tabbatar mata da sai ta je ai shi zumunci yake so da ita ba tsiya ba, wanda yake sonka da arziki kuwa ya gama maka komai da babu inda zata je ai zama lafiya ya fi zama ɗan sarki. Ko da ta dawo da ɗakin Mammin ta fara ta duba jikinta suka ɗan yi hira kan ta wuce ɗakinta aka biyo ta da abinci, sai da ta ci kan ta shiga tayi wanka da alwala ta zo tayi sallah, a gaban mirror ta zauna tana kallon kanta a yanzu ko ita ta san ta yi kyau, ta ɗan yi ƙiba skin ɗinta na wani irin yalki don man da Abeeha take shafawa ita ma shi ta saya mata kuma skin tone ɗin su ɗaya, ta sake cika tayi kumatu kaɗan sai ya mata kyau, kwalli ta zana a idanunta bata cika sakawa ba amma ta san yana mata kyau kawai dai bata son sakawa ne don yana sa idanunta hawaye sai wani ruwa ya kwanta ciki kaman mai, dama gasu da girma masha Allah, lip gloss ta shafa ta miƙe ta tafi gaban wardrobe. Abaya ta ɗauko wani blue da adon fari egyptian ne ya amshe ta sossai ta saka farar hula don farin gyale yake da shi sai ta yafa gyalen ta yi kyau sossai sai ta ji nishadi a ranta, wa zai ganta ya ce Afeefar Dutsen-wai ce, Mayya kuma annoba? Wa zai ce tagayyara aka so tayi Allah ya dube ta ya tallafi rayuwarta? Malamin islamiyyarta na makaranta na cewa Allah zai buɗe ma bayinsa kokafofin rahama da sauƙi cikin ko wani tsanani muddin ka saka tsoronshi da tawakalli cikin ranka, sannan zai buɗe maka kofofin arziki ta inda baka yi zato ko tsammani ba ko a mafarki bata zaci ganinta cikin irin wannan gida tana rayuwa ba, tayi tunanin za ta tabbata a bauta da wahala a kasakance amma da Allah ya ce ba hakan bane ga inda ya kawo ta a yanzu. Da kyar ta bar gaban madubin wurin Mammi ta nufa. "Masha Allah Daughter ta tayi kyau tabarakallah!" Murmushi tayi tana zama gaban Mammin "Mammi zolaya ta fa kike ina kyau anan? Ko fa powder ban shafa ba" Mammi za ta yi magana kenan Abeeha ta shigo kaman ta jima da Dawowa don ba da kayan da ta fita ta shigo ba. "Afeefah Dr. Sulaiman ya kira yana harabar gidan nan" Mammi tace "Abeeha gobe dai tunda saturday ne ku je ki nema mata waya mai kyau" Murmushi Afeefah tayi tana Miƙewa "Sai kun dawo a gaishe su, sannan a kula. Abeeha kar ku jima kin san Yayanku" Da Toh duk suka amsa suka fice daga parlorn. Ta jima sossai tana tuna Afeefah a ranta kan ta sauke ajiyar zuciya tana Miƙewa da kyar cikin yanayin rashin ƙarfi da cikakken lafiya ta shiga cikin ɗaki. A harabar gidan kuwa suna fitowa Rayyan na parking, gaban Afeefah ne ya faɗi zuciyarta ya shiga doka wa da ƙarfin gaske, a natse ya buɗe murfin motar ya sanyo jikinshi waje Farar jallabiya ce da daga ganinta zaka san tana da tsada sai maiƙo take yi kirar Kasar dubai don tana da wani ado mai yanayi da rubutun larabci daga gefen kirjinshi kaɗan har karshen hannun hagunshi, hirami ne baƙi mai layi layi fari ya mishi wani ɗauri a kai yadda Larabawa suke yi ya zauna mishi sossai yayi kyau, kafafunshi sanye da halfcover Milano baƙa, hannunshi na daure da wata silver agogo yayinda zoben azurfan dake yatsar shi na kusa da ƙarshe ke ta daukar idanu. Kallon duk a seconds biyar ta yi mishi don fargaba da ta kan tsinci kanta a duk arean da yake, baƙar shade na maƙale a idanunshi ba za ta san ya ko kalli iskar da ya kwaso su ba yau ko Sulaiman dake zaune cikin mota bai kalli sashen da yake ba ya shige gidan kamshinshi na buso musu, Abeeha ce ta iya yi mishi "Sannu da dawowa" Hannu kawai ya ɗaga mata wai shine amsar ya shige abunshi. Motar Sulaiman suka isa Afeefah ta shiga gaba Abeeha ta zauna baya suka fice daga gidan suna sake gaisuwa. Har suka isa shi ne yake hira da Abeeha ita kam tana zaune shiru, shi ya musu iso har cikin gidan Baaba ta taso ta rungume Afeefah dake ta murmushi a ƙasa ta zube tana gaishe da mahaifiyar shi Umma ta miƙa mata hannu ta je kuwa ta kama sai ta zaunar da ita gefenta tana ɗan rungumeta kaɗan "Ina ta jin labarin ɗiyata sai yau Allah yayi zan ganta! Barka da zuwa barka da zuwa" Murmushi Afeefar ke ta yi hakika ta ji matukar daaɗin irin tarbar da ta samu, kayan kwadayi da su drinks aka cike musu gaba da su ita dai kunyar Ummar take ji yadda take ta jansu da hira shi Sulaiman ya fice Sashenshi da a cikin gidan yake. Sun jima sossai har aka yi la'asar suka je suka gabatar suna dawowa parlorn Su Fauza suka fito shirye don wucewa islamiyya suka yi sallama akan su ma za su zo musu suka fice, basu jima da fita ba sai ga Sulaiman da matarshi sun shigo, kyakyawa ce kuma fara tasss bata da wani girman jiki a shekaru kuma da kaɗan za ta iya fin Afeefar kila su yi sa'a da Abeeha, zama tayi tana ce musu sannu. Gaisawa suka yi kadaran hadaran, tunda ya ce mata da Afeefah yake ta zuba idon ganin Afeefar da bata santa ba amma ta yi matuƙar haddace sunan saboda yawan Ambaton da Sulaiman ke yi musamman in tayi wani abu, sai ta ga Afeefar ma ba wai kyau ta fita ko ado ba haɗiye abin da take ji tayi ta yi musu sallama ta fice. Baaba ce ta kawo zancen su kawu tana tambayar Afeefah me yasa suke kiranta annoba? Shiru ta ɗan yi kan ta shiga basu labarinta daga farko har ƙarshe, Baaba da Umma sun sha kuka umma ta sake rungumeta tana cewa "Sannu Afeefah... Sannu! Allah ubangiji ya ƙara miki karfin zuciya da imani ya wanke miki duk wannan wahalhalun" Ta amsa da Ameen tana murmushi don a wannan karo bata yi kukan ba illa iyaka Adu'a da tayi ta bin iyayenta da Aunty zee. Sulaiman dai bai iya ya ce komai ba a ranshi yake ayyana Dole ta sha piya-piya don kashe kanta, dole ta samu saukar jini don damuwar, ya so da ita ce a ɗakin shi a yanzu matsayin matarshi ya bata duk wata kulawar da ta dace amma gani yake lokaci ya riga ya ƙure, Dukda haka zai zauna matsayin yayanta zai bata duk wani gudumawar da ya dace a rayuwarta daga yanzu. Karfe hudu ya maida su sun bar gidan da tsaraba niki niki daga Umma ta kuma roki Afeefar da ta dinga zuwa mata, har cikin gida ya dawo dasu suka yi mishi godiya suka nufi ciki. **** Karfe 3:40 ya fito ya wuce masallaci sai wuraren 4:20 ya koma cikin gidan kai tsaye sashen Mammi ya nufa don ya duba ta, tana zaune kan sallaya sai dai kanta na kife ne a bakin gado, da ɗan hanzari ya isa gareta "Mammi! Lafiya kike kuwa?" Ta ɗago ta sakar mai murmushi ya runtse ido da ƙarfi, da gaske murmushi take sai dai a cikin murmushin wani irin ciwo yake hanga da damuwa haɗe da gajiya, a idanunta wani abu mai wuyar fassara yake karantowa, tausayi da rauni suka rufe shi wanda basu ɓuya ba sam don a kan Mammi baya iya danne damuwarshi. "Saraki..! Ina lafiya, ka zauna za mu yi magana" A gabanta ya zauna kasancewar akwai turkish center carpet mai tsananin taushi da tsada dake malale tsakar ɗakin. "Ina muka kwana da zancen mu? Saraki babu lafiyayyen namijin da zai iya dawwama ba tare da mace ba, aure na sani ba dole ba ne amma babbar sunnah ce ta ma'aikinmu sannan akwai wani hadisi da Manzon Allah yayi magana akan bayan mutuwar mutum komai nashi zai tsaya chak sai abu guda uku, sadaka mai gudana, ilimin da ya samu ya kuma bayar da shi sai ɗa nagari mai mishi Adu'a ashe baka Fatan ka ajiye 'ya'yan da za su yi maka Adu'a bayan baka nan? Bana so in sake ji ka ce min ba zaka taɓa aure ba wanchan kuskure aka samu da akasin rashin sanin nagarta da kyaun halinka... Ba duka aka taru aka zama ɗaya ba" Kallonta kawai yake idanunshi duk sun sauya sun zama red har jijiyar kanshi na tashi, sam baya so baya son jin zancen wani aure daga bakin Mammi, a baya dai ya so yi amma bai san mummunar taɓonshi zai sa a hana shi aure ba, bai san za'a iya kallon cikin kwayar idanunshi a faɗa mishi kalmar da har abada ba zai taɓa mantawa ba, baya so a maimaita baya so samm. "Mammi..." "RAYYAN...!" A razane yake kallonta jin yadda ta katse shi, ta katse shi da asalin sunanshi da bata taɓa ƙira ba... Gabaɗaya sai hankalinshi ya sake tashi a raunane ta ce "Rayyan kana so in mutu ban ga ka samu cikakkiyar natsuwa da kwanciyar hankali ba? Kana so in tafi wurin ubangiji ina tunanin rayuwar ka zai iya taggara bayan babu ni? Kana so in tafi in barka ban cika alkawarin da na ɗauka wa rayuwarka ba?" "Yaaa ilaihil alameen..." Ya faɗa a rikice sai ya miƙe tsaye don wani irin tashin hankali yake ji, taku biyu yayi gaba ya juya yayi biyu baya yana shafa kanshi zuwa fuskarshi ji yake kaman ya tsala ihu ko zai fahimtar da Mammi abin da yake ji a cikin zuciyarshi. Zama yayi ya kalleta "Mammi saboda ke don ke kaɗai zan amince da zancen aure! Amma ban san kuma ta yadda zan je in cewa mace ina sonta ba, ban ma san menene son ba, ban san ta ina zan fara ba kuma... Na bar miki, na bar miki wuka da nama duk abin da kika yanke ni mai karɓa ne" Shiru tayi tana kallon shi, ya riƙo hannunayenta "Mammi kin san yadda na ɗauki alƙawari, na miki alƙawari zan yi iya kokarina a duk abinda za ki yanke a kaina, wanene ni da ba zan miki biyayya ba a duk abin da kike so? Ki kawo ko wacece zan zauna da ita yadda kike so matuƙar hankakinki zai kwanta, matuƙar za ki daina yi min zancen tafiya ki bar ni... Mammi kika ci gaba zuciyata za ta iya tarwatsewa" Hawayenta ne suka zubo, ta gimtse hannunshi dake cikin nata tana murmushi a lokaci guda ko babu komai zai tuna da ita ta zaɓar mishi mata, zai tuna da ita ya yi mata adu'ar alkhairi a duk sadda zai ga wannan mata ya ji farin ciki, in shaa Allahu ba zata yi zaɓin nan da kanta ba za ta bar wa Allah, za ta tsaya tsayin daka ta roƙi ubangiji yayi mishi zaɓi da kanshi ta san sai ya fi dacewa duniya da lahira... Anan suka bar maganan ya miƙe ya fice, ta bishi da kallo ta tabbatar yau bacci rabi da rabi zai yi hannu ta ɗaga sama tana cewa "Allah ga bawanka nan Rayyan! Allah ka sassauta mishi Allah ka yaye mishi matsalarshi Allah ka sada shi da duk wani farin cikin wannan duniya ka bashi dacewa a ƙiyama..." Ta shafa. Daga wannan rana Mammi ta dukufa adu'ar neman zaɓin Allah, ko sau daya bata yi tunanin wata mace ba damuwarta kawai Allah ya zaɓa mishi mafi alkhairi cikin mata, ya zaɓa mishi matar da za su tabbata har a aljannah wacce zai so ta, wacce idan ta tashi barin duniyar za ta kular mata dashi ta yadda ba zai yi kukan rashin ta ba don har a yanzu jin Rayyan take kaman yaro ƙarami da kan riƙe hannunta yayi kuka yayi kuka matuƙa idan an faɗa mishi abin da ya taɓa zuciyarshi, har yanzu ganinshi take kaman wannan dakakken yaron mai tsananin juriya da ƙarfin hali wanda duk wani abin da zaka mishi baya bari a ga rauninshi sai in yana gabanta. Ta ɗauki tsawon sati biyu tana wannan roƙon Allahn a cikin uku bisa ɗayan dare lokacin da Allah ya ce mu roƙe shi zai amsa mana, lokacin da ubangiji ke sama na ɗaya yana neman bayinshi masu roƙon shi ya amsa musu babu hijabi, a yau daren Alhamis safiya juma'a bayan ta gama nafilfilunta ta kwanta kaɗan saboda dan ciwo dake damunta a ciki, dole bacci ya lallaɓa ya dauƙeta ana ƙiran farko na assalatu ta farka a ɗan firgice ta miƙe zaune, a hankali ta saki murmushi mai kyau kan tayi Adu'a ta miƙe ta nufi bayi don gabatar da Alwala. 🖤Gureenjoh🖤 HAIHUWA DA HANJI (A True life story) Fatima Muhammad Gurin (Gureenjoh) Wattpad-Gureenjo6763 Arewabooks-Gureenjoh *FREE BOOK* *Comments ɗin ku shi zai yi determining Page na dare%* *28* Tun ƙarfe goma sha ɗaya na safe Rayyan ya bar office don ya je da wuri yau din saboda wani aiki da ya taso, gida straight ya koma yayi wankan juma'a don yana so ya fita da wuri yana so ya fara biyawa wurin salim da ya rasa gane kanshi a kwanakin. A shirye ya fito cikin shigan manyan kaya don fa shi yana son manyan kaya haka kawai bai cika son sa kananun kaya ba kaman yadda yake saka manya ɗin, governors yard ne da aka yi wa dinkin zamani ya zauna mishi sossai da sossai, ko da ya fito ɗakin Mammi ya fara yi ya sameta zaune tana azkar ɗinta da bata rabo da shi. "Sannu da hutawa Mammi" Ya faɗa yana zama gefenta "Sannu Saraki ashe ka dawo har ka yi wanka" Ya gyaɗa kai "Ina so zan fita da wuri ne zan biya wurin Salim" "kwana biyu kam bai shigo ba, ko da shike lafiya shi ke ɓuya ko?" Murmushi kawai ya ɗan yi zai yi magana sai ga Afeefah ta shigo hannunta riƙe da tray mai dauke da plate na abinci. Bata san yana nan ba da bata shigo ba don fa ita duk abin da zai haɗa ta dashi kiyayewa take saboda yadda bata samun natsuwa a area ɗin da yake gashi abin laifi baya mishi kaɗan yanzu ya hau faɗa da masifa, a gaban Mammi ta ajiye tray ɗin ya bi trayn da kallo kan ya kalli Mammi dake godiya ya ce "Ba dai wannan abin za ki ci ba?" Daga ita har Afeefah kallonshi suka yi abinci ne ya zama abu? "Me yayi?" Bai amsa Mammi ba sai Afeefah da ya kalla da idanunshin nan yace "Kashe ta kike son yi?" Wani irin faɗuwa gabanta yayi jin zancen kisa, hankalinta sai ya so tashi idanunta duk ta zaro waje tana so tayi magana amma Muryar rawa yake, tana da trauma na batun kisa da ita kanta bata sani ba, amma yadda ake jefanta da kalmar kisa yayi affecting mind ɗinta ta yadda ko ya aka ambaci kisa aka danganta ta da shi sai hankalinta ya tashi. Tsawa ya daka mata cikin muryarshi da ke razana ta "Na ce kashe ta kike son yi? Me yake damun ki da za ki dafa kowani shirme ki kawo mata?" Ganin yadda ta sake firgita Mammi ta dafa shi. "Saraki...! Wai me haka ne? Meyasa kake haka? Idan ka bi ta a hankali ai za ta fahimta ba sai ka yi mata faɗa ba, kuma ni na saka ta dafa min ba gaban kanta tayi ba" "Mammi ina Merry?" Yayi tambayar ranshi a hasale, idan da bayanan sai Mammi ta ci abincin nan don ya tabbatar ko don wahalar da wannan yarinyar tayi ta dafa zata iya ko loma kadan ne don yarinyar ta ji daaɗi, Dukda Couscous ne amma akwai abubuwa masu yawa da bai kamata ta saka mata ba ciki. "Merry bata ji daaɗi ba jiki da jini, Abeeha na school shiyasa nace ta dafa ɗin amma na tabbatar bata gane bayanin da na mata bane ba da gangan tayi hakan ba" Tsaki ya ja ya ɗauki tray ɗin ya fice. A ƙasa ta zube tana sauƙe numfashin tsoro yadda yake zaro mata ido kawai take gani, Mammi ta dafa ta "Ki yi haƙuri Afeefah duk ya firgitaki" "Mammi ban san akwai abubuwan da bai kamata ki ci ba ciki kiyi haƙuri laifina ne" "ba wani laifin da kika yi na kirki Alaiyahu da kuma tomatoes da kika saka ciki duk are high potassium veggies da bai kamata in ci ba su ne fa kawai sai zubin da yayi yawa kasancewar Couscous ɗin daga wheat ake samun shi, amma ai ina da ido kuma zan iya miki gyara shi dai kawai zafin kanshi ne dayawa" Dukda halin da take ciki sai da ta ɗan murmusa kaɗan, yau public holiday shiyasa bata je school ba itama Abeeha wani research take yi shiyasa ta tafi Merry wacce ke da karatu na musamman akan nutrition ɗin irin masu ciwon Mammin bata da lafiya shiyasa ta shiga kitchen ɗin ta girka ba wai don gwaninta ko nuna iyawa ba, jikinta ya yi sanyi bata ma zauna wurin Mammin ba ta fice kar ya dawo ya sameta. Shi kam kitchen ɗin ya koma, a hankali masu aikin suka zame suka fice sanin kila da kanshi zai yi girkin kaman kuwa sun sani, a take ya fara shirya abincin Mammin, idan ka ga yadda yake aiki za ka zaci wani professional Cook ne cikin taka tsantsan da tsantsar tsafta da Allah yayi mishi, wanke hannu kuwa ko me ya taɓa sai ya je ya wanke hannu da handwash ya dawo, ko sau ɗaya kayanshi bai taɓa komai ba har ya gama ɗan small portion na chicken salad wanda da breast ɗin kawai yayi amfani duk wani ƙashi babu ciki, babu gishiri ya gasa da herbs kawai da lemon, ya haɗa salad din wanda lettuce ne sai cucumber da Bell peppers da albasa kaɗan, ba mayonaise ko cream ya saka ciki ba sai ya zuba man zaitun pure one a cikin dan karamin bowl ya saka 1 tsp na vineger ya kaɗa da 'yar habbatussauda kaɗan ya juye a cikin salad din ya gauraya ya zuba a cikin wani bowl mai kyau. Shinkafa ce 'yar kaɗan ya dafa mata half cup ya haɗa da ruwa don bata shan wani sugar ko juice ya ɗauka ya nufi ɗakinta. Murmushi ta saki tana mishi godiya, ita bata yi mamaki ba don kafin yayi hiring merry da kanshi yake yi mata duk abinda zata ci shi ya uzzurawa su Abeeha har suma suka iya duk cimar ta da yanayin awon duk sun haddace, godiya ta mishi yace "Mammi babu fa wannan tsakanin mu har Abada, abin da ya zama min dole ne nayi" Daga nan ya mata sallama ya koma ɗaki ya sake gyara jikinshi kan ya kara turare ya fice daga gidan. Kai tsaye gidan su Salim yayi, kasancewar yanzu ba kaman da ba ta babban parlor ya shiga da sallama, Mommy da ke zaune ta zabga tagumi ta ɗago ta amsa a hankali, ya zamu wuri ya zauna yana gaisheta "Lafiya ƙalau Rayyan ka shigo?" Samha dake kuka ya ɗan kalla kan ya kalli mommyn "Lafiya kam mommy?" "Ba ƙalau ba Rayyan, ban san me zan ce ba ban kuma san ta ina zan fara ba amma tabbas Salim baya cikin lafiya da natsuwar shi... Rayyan ko za ka bashi shawara? Ko zaka mishi faɗa? Don saleem bai ɗauke ni uwa ba kuma, saleem ya fi gane maganar matarshi akan nawa yanzu ya bar nan bayan ya fasa bakin Samha don kawai ta roƙe shi kuɗin makaranta suna shirin exams bata biya ba matarshi ta sa baki sai tace mata ba da ita take ba da ɗan uwanta take shikenan har ya kai abin duka kuma yace ba zai biya ɗin ba rashin kunyarta ya biya mata? Saleem dai ina mishi magana ya ɗaukeni banza? Innalillahi wainna ilaihi rajiun..." Wasu irin hawaye masu zafi take zubarwa bata taɓa zato ko tsammanin irin wannan butulcin daga Sabrina ba, shi karan kanshi Rayyan yayi mamaki don kowa ya san saleem ya san yadda ya ɗauki mahaifiyarshi da ƙannenshi, shi ɗin mai biyayya ne ko da ko baya so zai yi don ya faranta ran mahaifiyarshi, ya san dai saleem ya chanza mishi amma bai zaci har mahaifiyarshi da yan uwanshi ba, sai ya kira shi ba zai ɗaga ba kuma ba zai kira shi back ba, sau biyu yana zuwa headquarter baya samun shi shiyasa ma ya yanke ya zo gida ya same shi, Dukda shi namiji ne kuma ba kaman sauran maza ba amma daga maganan mommy ya fahimci akwai ayar tambaya mai girma akan saleem. Bai gama tunanin ba aka fara sallama, sameerah dake zaune shiru gefe ta miƙe ta nufi kofar. "Mun zo daga companyn gadaje da kujeru ne mun kawo order ɗin da aka sanya wannan address ɗin..." "Anya gidan nan ne? Ko zaka kira Layin da aka yi order ɗin?" "Toh bari na ƙira" Kira yayi cikin mintuna biyu sai ga saleem da Sabrina sun sauƙo, ganin Rayyan ya sa ya je ya bashi hannu suka gaisa "Saleem kana lafiya?" Yayi tambayar yana sake nazartar abokin nashi da ya ji wani irin tausayinshi ya tsarga mishi. "Lafiya me ka gani?" Girgiza kai kawai yayi ya ce "Zauna za mu yi magana" Babu musu saleem ya zauna Sabrina za tayi magana ya ɗaga idanu ya zuba mata haka kawai kwarjinin shi ya wani irin cika ta, duk yadda ta so tayi magana kasawa tayi sai ta nufi kofa ta fice tana kwafa. "Me ya sameka? Me ke damunka abin da baka yi ba tun kana ƙarami zaka yi shi yanzu da ka mallaki hankalin kanka? Saleem uwa ba Abar wasa bace ba kowace uwa ba, ba irin mahaifiyarka da tayi dedicating lafiyarta, karfinta da kuruciyarta don ganin ta gina rayuwarka ba... Ta gina ka ne don ka girma ka tallafi kannenka, yau idan baka biyawa su Samha kudin makaranta ba wa kake tunani zai biya musu? Me ya hau kanka haka saleem?" A tausashe yake maganan, saleem bai ce komai ba ya zauna shiru duk yadda Rayyan ya buga ya kaɗa akan ya faɗa mishi menene matsalar bai ce komai ba, daga karshe Rayyan ya ce "Saleem ka ba Samha kudin makaranta yadda ka saba bata" Ɗago ido yayi ya kalleshi shima shi yake kallo zuciyarshi na rawa, tabbas akwai ayar tambaya akan dabiun saleem sai dai ba zai yi saurin yanke hukunci ba, yana zaune nan sai da saleem ya dauki tsawon mintuna biyar kan ya zaro wayanshi yayiwa Samha transfer ɗin kudin yadda ya saba bata, mommy ta duƙar da kai tana kuka mai ciwo. Da zafi abin da zafi kana gani a sauyawa danka rayuwa daga yadda yake zuwa wani abu daban. "Je ka shirya mu tafi masallaci" Bai ce komai ba ya miƙe ya haura sama, Rayyan ya runtse ido a hankali sama da seconds goma ya buɗe sun dan sauya, Miƙewa yayi ya fice bai kula godiyar da mommyn ke mishi ba, a gaban motar shi ya tsaya yana kallon Sabrina da ke tsaye ana sauƙe wasu kwalaye cikin store nazarin ta sossai yake yi chan ya ɗauke idanu ya sauƙe kan saleem da ya fito, yana kallo sai da yaje wurinta suka yi magana ta ɗaga ta kalleshi kan ta gyaɗa kai saleem ya wuce ya zo ya shiga motar suka fice daga gidan. "Saleem idan ka ga Afeefah a yanzu za ka iya aurenta?" Shi karan kanshi bai san ya jefawa saleem ɗin tambayar ba don ya jima yana mishi yawo a rai kuma yana son tabbatar da zarginshi kan Sabrina. Sunan Afeefah ya sake maimaitawa a ranshi don dai bai taɓa ambatar sunan a fili ba ma sai yau. "Aure? Ai ina da aure" Ya amsa shi muryarshi babu wannan karsashin idan yana maganar da ya shafi Afeefah, kaman ma wata ce chan daban da bai wani sani ba. Bai ja maganan ba ya yi shiru, dole su tashi tsaye akan Saleem da alama zautar da shi ake shirin yi, amma yayi matukar mamaki irin mamakin nan da bai taba zaton hakan zai iya faruwa da saleem daga aure ba, auren ma na dangi ba bare ba. **** Zaune take gaban Mammi don sai da ta tabbatar ya fice kan ta dawo, abincin ta tsurawa idanu yadda ya tsara shi kaman wani chef tana mamakin yadda ya iya girki haka, Mammi bata ce komai ba ta shiga cin abincin sai da ta gama tsaf ta dubi Afeefah tace "Afeefah akwai maganar da nake so mu yi da ke ko kuma in ce akwai alfarmar da nake so na roƙe ki ban san ko za ki iya yi min ba, ba abu bane da ya saɓawa shari'ar musulunci abu ne da muddin kika amince min Afeefah zan yi matuƙar farin ciki fiye da zaton ki" Afeefah ta gyara zama jin maganar serious ne, kuma a yadda Mammi ta ɗauke shi da muhimmanci ya sa itama ta ji ta bashi muhimmanci itama "Tashi ki dawo nan Afeefah" Miƙewa tayi ta koma kusa da ita yadda ta roƙa hannayenta duk biyu ta riƙe "Afeefah na dauke ki ne tamkar Abeeha, ba zan taɓa yin wani abu da zai cutar da rayuwarki ba amma ban san yadda za ki ɗauki maganar ba.." "Mammi yanzu fa kika ce ni tamkar Abeeha ce a gareki nima kuma ba ni da uwar da ta wuce ki, wlh duk abin da kike so matuƙar zai faranta miki kuma bai saɓawa shari'a ba ni mai amincewa ne Mammi, faɗa kawai za ki yi in cika shi na san ba za ki taɓa cutar da ni ba." Afeefah ta katse ta ganin kaman contemplating take na gaya mata abin da take so, ita kuma tana da yakinin koma menene Mammin za ta roƙa ba sharri bane. "Afeefah za ki iya auren Saraki??" Afeefah ji tayi kaman kunnenta bai ji mata daidai ba, bata motsa ba don bata gama fahimta ba jin Mammi ta yi shiru tana kallonta yasa tace "Mammi ina sauraranki in shaa Allahu zan yi duk abin da kike so" "Afeefah abin da nake so shine kafin na mutu in ga na haɗa aurenku ke da Saraki...! Shin za ki iya auren shi? Za ki iya yi min wannan alfarmar?" Wani irin shock ne ya ratsa Afeefah daga kanta har cikin tafukan sawayenta, a matuƙar razane ta zare hannunta daga na Mammi ta miƙe tsaye zuciyarta na wani irin bugawa kaman zai ratso kirjinta ya fito "a..ure? Ni Mammi? Ni... Ni Afeefah da Wanchan mutumin...??" Don ji tayi ba zata iya ƙiran sunanshi ba ma ko Rayyan ɗin ko Saraki idan tayi hakan kaman wani zunubi ne da muddin ya ji ta sai ya sauya mata kammani, kallon kanta take yi daga sama zuwa kasa ta ɗago ta kalli Mammi kaman wacce ta zauce... 🖤Gureenjoh🖤 https://chat.whatsapp.com/BuI7cmoy3ed3C3IimZKZA0 HAIHUWA DA HANJI (A True life story) Fatima Muhammad Gurin (Gureenjoh) Wattpad-Gureenjo6763 Arewabooks-Gureenjoh *FREE BOOK* *29* Hasaso Rayyan ɗin ta shiga yi a majigin kwakwalwarta, kallo ɗaya tak za ka yi mishi ka san cewa shi ɗin soja ne a sojojin ma na daban, yana da lafiyayyar jiki murɗaɗɗe kuma a tsaye yake fatarshi babu ɗigon baƙi ko guda ɗaya, Dukda ba zata ce ga yadda yake cikin khaki ba amma ko daga maganar shi zai tabbatar maka jajirtacce ne kuma gwarzon namiji wanda ko daga kallonshi za ka sha jinin jikinka. Zaman shi, tafiyar shi da yanayin dabi'unshi kuwa za ka zaci wani babban sarkin ne na wani yanki na daban, yana da wasu irin idanu kyawawa da ko tuna yanayinsu tayi sai ta ji tsikar jikinta ya zuba kaman ba namiji ba, fasalta kyaun fuskarshi da sauran halittar da Allah yayi mishi ma wani tulin bayani ne na daban, don Allah ina ita ina irin gawurtaccen nan? Ta ina ma Mammi ta fara wannan tunanin? Tazarar da ke tsakaninta da Rayyan kaman tazara ne da ke tsakanin sama da ƙasa ko ta amincewa aurenshi ita ce zata wahala daga karshe saboda ba zai taɓa son irin ta ba, ba zai taɓa kaunar mace kamar ta ba wacce ta fito daga kauye cikin tsantsar jahilai, wacce take da tambarin Maita kuma annoba, wacce ko wucewa ta zo yi gidajen mutane sai an zuba tafarnuwa, Ƙashin kifi da garin kukan miya a wuta don hayaƙin Mayu.... Ai ko da gami wane ita da Rayyan. "Mammi kaman ban ji abin da kika faɗa ba" Ta sake maimaitawa har yanzu a kidime. Miƙewa tsaye Mammi tayi ta riƙo hannunta suka koma zaune. "Ki natsu Afeefah kin ji? Ki ba ni hankalinki kar ki yi wani tunanin fin ƙarfi, namiji bai taɓa fin karfin mace ba in har ta amsa sunanta mace, ke kyakyawace kar kyaun Rayyan ya ruɗe ki, ke yarinya ce mai hankali, ladabi, natsuwa da kuma biyayya kina da zuciya mai kyau, you are the purest soul i've ever met... Afeefah ba zan hada ki da Rayyan bane saboda wani ra'ayi nawa ko buri eh ina da buri a kan ku duk biyu, sai dai burin ba na komai bane sai na son ganin rayuwarku duk ya inganta kun tabbata cikin farin ciki" "Mammi shi ya ce miki yana so na?" Ta tambaya a sanyaye don ba fahimtar kalaman Mammin take ba don abu ne da take ji ba zai taɓa yiwuwa ba. "Ba shi ya ce ba, ni ce na ga cancantar kasancewarku inuwa ɗaya kar ki damu da halinshi ko yanayinshi na fushi da dacin rai Saraki na da wani tabo ne da ya mayar da shi hakan wanda dole zan faɗa miki Afeefah... Ina so in fada miki ba don tonon asiri ba, sai don ya zama dole ki sani kan ki yanke shawarar za ki aure shi ko ba za ki aure shi ba? Ba zan miki dole ba wlh kuma ba na so ki dube ni a yayin yanke hukunci ki yanke duk abinda ke ranki ni me karɓa ce don sai da na nemi zaɓin Allah kan na tunkareki" Shiru Mammi tayi idanunta sun rine sossai har suka tara hawayen da ya fara bin ƙuncinta, ɗacin maganan da zata faɗa take ji har kan harshen ta maganan da bata taɓa faɗa da Bakinta ba bata taɓa ambata ba sai a yau da ya zame mata dole, idanunta na kallon gefe ta furta "Rayyan ba ɗa na bane!!!" Wani irin bugawa zuciyar Afeefah yayi da har sautin shi na fitowa fili ta zaro idanu gabaɗaya tana kallon Mammi dake ta zubar hawaye "Eh Afeefah ba ni na haife shi ba, hasali ma babu abin da ya haɗa ni da shi na jini ko na kusa ko na nesa... Ni sunana Khadija ni haifafffiyar wannan gari ce ta Kaduna, mahaifina Alhj Isma'il mai rasuwa mutum ne mai tarin dukiya mai yawa a gaske kuma su biyu Allah ya ba wa iyayensu ɗan uwanshi ma na da nashi arzikin don gada suka yi, mahaifina mutum ne da dukiyar shi bai taɓa rufe mai ido ba, yana da kyauta tsantsa haka yana da taimako don haka ko da na zama ni kaɗai 'yar shi yana da ƴaƴa dayawa da suke karkashin shi don lakabinshi ma shine Uban marayu da masu uba... Yaran da ya biyawa suka karatu basu kirguwa sai dai in baki zo wurinshi da kuka ba sai ya share miki hawaye, wannan dalili ya sa nima na taso da irin zuciyarshi Dukda rashin lafiyarmu don shi ma ciwon sugar ne ya kashe shi kaman yadda ya kashe baban shi, ƙannunshi ma Uncle Musa haka yake don suna da nasaba mai kyau suna da ilimi boko da arabi. Akan irin rayuwar da na tashi kenan har na kamallah jami'a ta ina da shekaru ashirin da ɗaya a duniya, wata rana ina driving na zo daidai wurin ba da hannu sai na hangi wani kyakyawan yaro da ba zai wuci shekaru shida ba yana da irin kyaun da in ka kalleshi sai ka sake da sauri ya zo ya shiga gaban motana ya fara wanke mini glass don kaman sana'ar da yake yi kenan a wurin ake bashi goma biyar na cin abinci, Dukda fuskarshi a matuƙar haɗe ko alamun dariya babu kayan jikinshi kuma basu ji jiki chan chan ba amma sun dan yi duhu kaman ana yawan tsoma su ruwa, bayan ya gama ya dawo gefena ya tsaya tsantsar tausayinshi ne ya rufar mini, wannan yaro ƙarami da ke bukatar ingantacciyar rayuwa yaron da bai wuce a ce yana gaban mamanshi a kwance ba shine ke wannan walagigi yana neman abin da zai sanyawa cikinshi, sauƙe glass din nayi muka haɗa ido na sakar mishi murmushi "Yaya sunanka?" Na jefa mishi tambayar ga mamaki na ko ci kanki bai ce ba banda idanu da ya tsura min yana kallo, ganin an ba da hannu sai na zari dubu biyu na miƙa mishi kaman ba zai karɓa ba sai ya karɓa ya juya ya bar wurin bai ce min komai ba. Har na dawo gida tunanin wannan yaro ne a raina bayan kwana biyu na kasa mantawa da shi haka na ɗauki mota na koma inda na fara haɗuwa da shi na ajiye mota na shiga yawon neman shi da ƙafa, na yi nema sossai kan na same shi zaune gefen wani juji ya haɗa kai da gwiwa Dukda uban ranar da ke dukanshi ko motsi bai yi ba, daga farin Fatan shi da yanayin sumanshi na gane shi don ya fi yanayi da Fulanin usuli, gangar shi na je na duƙa na taɓa shi ya ɗago ya kalleni da idanunshi da suke a matuƙar rine fuskarshi yayi jazir, dabiun yaron sai bai min yanayi da na sauran yara ba don idanunshi na nuna wasu al'amari da na kasa fahimta, maganan duniya na mishi bai ba ni amsa ba sai ido na miƙe na je wurin wani mai wankin mota a kusa da wurin na nuna mishi yaron "Malam Don Allah wanchan yaron baya magana ne?" "Hajiya yadda kika ganshin nan haka mu ma muka ganshi kuma in za ka mishi maganar duniya ba zai amsa ba amma kin ganshin nan idan ya kwana da kayan jikinshin nan da safe zai zo ya ba ni goma in bashi ruwa da bokiti ya kwaba omo ya wanke zai zauna daga shi sai karamin wando idan ya bushe zai saka ya cire wandon ma ya wanke ya mayar da kayan, kin ga inda yake zaunen nan idan ba zai fita neman kudin abinda zai ci bane bai taɓa barin wurin ba sai wanka ko wanki da ya kan zo nan" Wani iri na ji har cikin raina, na mishi godiya na bar wurin na koma wurin mota na tafi na je na sayo duk wani abin makulashe da na san yaro zai buƙata na dawo na bashi ya ƙi karɓa a ƙarshe ajiye mishi nayi na tafi, Washegari na sake komawa don tausayi da kaunar shi ya riga ya samu gurbi a zuciyata, a ranar takalmina na cire na yi irin zaman da yayi nima Dukda ina jin zafin ranar minti minti sai ya ɗan waigo ya kalleni ban ce komai ba shima kuma bai ce komai ba, har dare ina tare dashi sallah kawai nake zuwa wani masallaci a wurin dake da ɓangaren mata abin da ya bani mamaki kuma shima haka zai je Sallar ya dawo ban tafi ba ranar ma sai da na sake cika mishi gaba da abubuwan cima kala kala, a takaice na jera kwana uku ina zuwa wurinshi a na huɗu ne ina zaune kawai sai na kama kuka, yayi shiru sai ya juyo ya kalleni kaman zai share chan dai na tsinci muryarshi kaman daga sama yana cewa "Me ya same ki?" Numfashi mai nauyi na sauƙe ashe ba kurma bane "Ba ni da lafiya ne kuma bana son zaman rana" Ga mamakina sai ya miƙe ya kama hannuna muka koma inuwa duk muka zauna bayan nan duk yadda zan yi yayi magana ya ƙi na sake yin kwana biyu muna zama a inuwa kan ranar kawai ya kalleni ya ce "Me kike so?" Ina mamakin yadda yake magana wane babba "Kai nake so in taimaka kai nake so in ɗauke daga wannan jujin in kaika gidan mu kayi rayuwa mai kyau, za ka bi ni?" Kallona kawai yake, ni kuwa ina hakan ne da zuciya ɗaya ba zan so rayuwar shi ya ƙare a kan titi ba ba zan so ya tashi a haka ba zai iya shiga ko wani hali. Kai ya gyaɗa min na yi farin ciki kwarai na kira babana ina mishi albishir don ya san labarin yaron har ya yarda duk ranar da yaron ya tanka ni kuma ya amince ya biyo ni ina da kyautar kujerar umura na yi farin ciki sossai da amincewarshi Dukda ba don kujerar ba saboda ko a lokacin na je Makka so ba adadi, na dauke shi daga nan muka dawo gidan mu. Ban barshi cikin ma'aikata ba na kaishi ɗaki na musamman na fita na yi mishi sayayya kan na dawo yayi wanka ya ci abinci na bashi kayan a hankali ya ce min "Na gode" Murmushi nayi a raina ina raya wannan yaro idan ya girma ba karamin mutum za'a yi ba don bashi da rawar kai irin na yara masu shekarun shi. "Ya sunanka?" "Ban sani ba" Abin da yace kenan na yi mamaki ƙwarai kuma kaman akwai abinda ya ɓoye min amma ban bincika ba nace "Zan saka maka suna amma sai na yi tunani sunana Khadija, mahaifiyata ta rasu ni kaɗai ce sai babana a gidan nan ka ɗaukeni tamkar mahaifiyar ka duk wani abin da kake so ni kuma zan cika maka shi ka ji?" Ya kalleni nayi murmushi "ban kai in haifeka bane? Shekarunka nawa?" Ya ɗaga min yatsu shida nace "To ka ga, da na yi aure ina 15 da na haifeka irin auren kauyen nan da ma ba'a kai hakan" Ya ɗan yi murmushi daga nan na fahimci shi mai ɗabi'ar miskilanci ne tsantsa babana na samu da shawara shi ya ba da sunan Rayyan in saka mishi ni kuma nake ce mai Saraki don ko sarki bana tunanin ya kai shi sarauta.. A lokacin gab aurena da baban su Jannah ne ko da ya zo shima farar daya son yaron ya shiga ranshi yayi alkawari zamu rike shi kaman mu muka haife shi ko da zan kaishi makaranta tare muka tafi da Mahaifin su Jannah shi yayi mishi komai aka ba da sunanshi Rayyan Mohd Khamis, bayan aurena da baban su Jannah bai fi da shekara ba Allah yayiwa mahaifina rasuwa ta hanyar ciwon sugar da ya sha fama da shi, na shiga tashin hankalin da Saraki ne kawai ke iya saka ni cin abinci kan daga baya na zo na watsakke don dama wannan dole ne, ranar da na haifi Jannah a ranar Saraki ya fara kirana da Mammi don tunda muke bai taɓa kirana ba ko zai yi magana sai dai kawai yayi na ce ko Aunty ya ce min ya ƙi, Rayyan bashi da lafiya don yadda yake ganin rana haka yake ganin dare idan yayi bacci kuwa haka zai yi ta wani irin juye juye yana haɗa gumi daga karshe cikin wani mummunan yanayi zai farka tun yana ƙarami muka fara ganin likitocin psychiatric su ma da kyar da pills ake samu yake dawowa daidai idan abin ya zo mishi especially lokacin zafi kasancewar a tsakankanin ne muka hadu. Baya so a mishi magana akan abin da ya kawo shi wurin ko iyayenshi tunda na fahimta ban sake yi mishi ba ko da wasa, irin kiyayewa da kular da muke bashi shine sanadin da ya sa ya samu ingantacciyar rayuwa yayi karatu mai zurfi har ya zama soja, bayan nan ne aka gano ina da Ciwon ƙoda Rayyan yayi fadi tashi kwarai har ƙodar shi yayi offering mini Mahaifinsu Jannah ya hana aka biya makudan kudi aka yi min dashe amma ba'a dace ba, a lokacin da nake jinyar Baban su Jannah ma ya rasu ga rashin lafiya ga rashin miji na yi ciwo sossai duk Rayyan ne yake tsaye tsayin daka a kaina ga ƙannenshi Jannah da Abeeha bai bari na tagayyara ba, yana mini son da iyakaci kenan ko da ni ce na haife shi. Saraki ya taso mai tsananin jarumta gashi dama magana ma bata dame shi ba don ko abokai bashi da su, sannan yaro ne da idan yana abu dole ka kalleshi yana da jin ƙai ko magana yake dole ka kalleshi, dalili na ya tafi short service a harkar lafiya don dama science ya karanta a secondary school, ba'a fi shekara biyu ba na matsa mishi da zancen aure ya nuna akwai wacce yake gani zai iya aure, magana ta fara nisa ranar ya je wurinta babanta ya zo ya same shi ya ce mishi "Ina so in ka koma ka tambayi asalinka sai a fara batun neman aure amma ba zan ba da auren ɗiyata wa marar cikakken asali ba" Wannan magana ya dake shi sossai, wanda ni na ɗan lallaɓa shi na tura uncle Musa sai ce mishi suka yi ba za su bada auren ba basu sani ba ko ba ɗan sunna bane ko an same shi ta gurbattacciyar hanya, magana ce mai girma a gareshi wanda ya tado ciwon baya da kyar muka samu ya dawo daidai bayan tsawon wata shidda baya bacci kuma ya ki faɗa mini wani irin mafarki yake ko wa Dr ɗinshi, gashi Rayyan baya taɓa zubar da hawaye, tunda ya girma rabon da in ga hawayenshi kila da wani abu zai ragu a zuciyarshi, daga nan yayi alkawarin ba zai sake neman aure ba don duk wanda ya sake kallonshi ya mishi gorin asali sai ya kashe mutum har lahira. Afeefah kin ji waye Rayyan, kin ji cewa bashi da cikakkiyar asali sai dai yana da tarin nagarta, ilimi, natsuwa da sanin ya kamata ga ibada tsantsa, yana da ni matsayin uwa da na bashi duk tarbiyar da uwa za ta iya ba yaro daga yarantarshi har girmanshi, ya samu gatan iyaye both uwa da uba don baban su Jannah har ya rasu bai taɓa nuna ko da da second daya cewa ba shine Uban Rayyan ba, kin ji cewa bashi da cikakkiyar lafiyar kwakwalwa ba na hauka ba sai na tsantsar damuwa akan abinda ya shafi rayuwarshi da ciwo a zuciyarshi wanda ya mayar dashi mai irin zafi da faɗan nan, tun yana yaro ba za ki taɓa ganin dariyar shi ba sai murmushi shima sai ya kama, shin za ki iya auren Rayyan a haka? Afeefah za ki iya yi min wannan alfarmar?? 🖤Gureenjoh🖤 HAIHUWA DA HANJI (A True life story) Fatima Muhammad Gurin (Gureenjoh) Wattpad-Gureenjo6763 Arewabooks-Gureenjoh ADABI WRITERS ASSOCIATION *FREE BOOK* *30* **Tana tunanin da kashe kai shi ne hukunci mafi sauƙi ga bawa a duk sadda ƙaddara ta ruro wutarta za ta samu miliyoyin mutane a raye ne?"** Da wani irin amo sautin muryarshi ke dawo mata a sadda yake faɗa farkawarta daga shan piya- piya, ashe da biyu yake yi mata irin wannan faɗan? Ashe shima duniyar ba daaɗi tayi mishi ba? Wasu irin ruwan hawaye ne ke bin fuskarta babu kakkautawa, sai taji har gwara ita ma da shi kaman ƙaddarar ta ya fi nashi sauƙi tunda tana kwanciya tayi bacci lafiya ƙalau, kuka kawai take yi duk yadda mammi ta so tayi shiru ta ƙi, sai da tayi ma'ishi Mammi ta bata ruwa ta sha kan ta ɗago ta kalli Mammi bata ce komai ba. "Za ki iya cewa Meyasa ban bashi Abeeha ko Jannah ba ko? Har raina na ɗauki Saraki ɗan da na tsuguna na haifa ne shiyasa har abada na haramta mishi auren 'ya'yana, uba yake a gare su a yanzu da basu da wani uba shi ya raine su bayan yana jinya na, shi ya basu tarbiya cikakkiya da har in sun fita ana sha'awar su. Wannan dalili ya sa ko da wasa wannan tunani bai taɓa darsar min ba don har in mutu bana fata ko sau ɗaya Saraki yayi tunanin don ba ni na haife shi ba zan iya ɓata mishi..." A hankali Afeefah da idanunta suka sauya ainun ta riƙe hannun Mammi "Ke mutumiyar kirki ce Mammi, kina daga cikin sahun 'yan aljanna in shaa Allah... Hakika kina da zuciya mai kyau wanda Allah ne yayi miki kyautar shi don samun irinki sai an tona" Murmushi kaɗan kawai Mammi tayi zata yi magana Afeefah tayi saurin cewa "Mammi ki bar roƙo na kin yarda da ni ni kuma in shaa Allahu ba zan ba ki kunya ba, wlh har raina na amince kuma zan yi iya kokarina in ga na ba da abinda ake so" Rungumeta kawai Mammi tayi cikin farin cikin da yake ratsa zuciyarta. **** Shi kam Rayyan daga masallaci ya mayar da Saleem gida bayan yayi ta mishi tuni akan mahaifiyarshi da 'yan uwanshi irin muhimmancin su a rayuwarshi duk yana ji amma amsawar wani iri, bai damu sossai ba don shima zai taya abokin nashi da Adu'a yana kuma da yakinin duk abinda yayi farko yana da ƙarshe musamman abinda ba don Allah aka yi shi ba. Daga nan gidan Jannah ya wuce, tana zaune kawai ta ji ana knocking ta tashi taje ta buɗe sai ta ganshi tsaye, murmushi ta saki tana mishi sannu da zuwa ya amsa yadda ya saba musu ya shiga ya samu wuri ya zauna, cikin mintuna kaɗan ta cika gabanshi da kalolin abubuwa su snacks da su abinci kan ta dawo ta zauna "Barka da juma'a Yaya" "Barka dai ya gidan?" Ta amsa da farin ciki "Lafiya ƙalau ya su Mammi?" "Alhamdulillah" Ya faɗa yana shan zobo don yana matuƙar kaunar zobo bayan ya sauƙe cup ɗin ya kalleta "ba ki da wani damuwa ko?" Kai ta gyaɗa "Babu komai Yaya" Ya ce "Masha Allah" Miƙewa yayi ya zare kudi ya ajiye mata dukda tana aiki godiya tayi ta mishi ta raka shi har mota ya tafi ta dawo tana murmushi ya kan yi hakan tun bayan aurenta, haka kawai sai ta ganshi zai zo ya duba ta ya tabbatar tana lafiya ya ajiye mata kudi ya tafi. Gida ya nufa kai tsaye, bai je Sashenshi ba don la'asar ya kusa yana so ya duba Mammi kan ya fita yayi sallah sai ya dawo ya huta gabaɗaya, ko da ya shiga yanayin wurin ya ɗan zubawa ido Dukda ya fahimci Mammi ta yi hawaye sai dai idanunshi da suka shiga cikin nata ya ɗan ji wani yanayi da har bai ɓuya ba, seconds ya kwashe yana kallonta kan ya ɗauke kai sai ta miƙe ta zo zata fita muryarta na cracking tace "Sannu da dawowa" Bata jira amsarshi ba ta wuce don ganinshi kaɗai tausayi yake bata. Ɗan shiru yayi kan ya taɓe baki yana ɗaga Kafada ya isa wurin Mammi "Mammi why did you cry? Yarinyar chan ne ko?" "Ni ce dai na sakata kuka ba ita ta saka ni ba, ka dawo?" Bai ja zaren zancen ba yace "Eh, hope baki ji yunwa ba?" "No ban ji ba, na san ma Abeeha ta kusa shigowa ko na ji ma zata zo ta sama min wani abin you should rest" Kai ya gyaɗa ya ɗan jingina da kujera yana lumshe ido "Ni ko ina son yin wata magana da kai" Buɗe idanun yayi yana kallonta "Saraki ka tuna kai ka ce in zaɓa maka mata ko ma wacece za ka aureta in dai ni ce na zaɓa?" Ɗan shiru yayi kan chan dai ya gyaɗa kai. "Toh mun samu Mata Saraki" Bai wani nuna ya ji daaɗi ko zumudi ba sai ma runtse idanu da yayi ya ɗan buɗe. "Baka tambayi wace ba kuma a ina?" "Mammi ke fa kika shirya wannan aure duk abubuwan nan ba lallai sai na ji ba ayi duk abinda ya dace kawai" "haka za ka aureta baku fahimci juna ba? Ai ba'a haka dole za ka nuna mata itama macece kaman sauran mata ka bata darajar ta na neman soyayya da ma kyautatawa da kan shiga tsakanin saurayi da budurwa" Idanunshi kawai ya zubawa Mammi don jinta kawai yake baya tunanin zai iya yin ko abu guda cikin wanda ta lissafo. "Mammi kin fa san duk ba zan iya wannan ba" "Toh na ji amma ka san wacece yarinyar? Ka dai san ba zan zaɓa maka wacce na san bata dace da kai ba ko? Kuma ka yi min alkawarin ƙarbar ta yadda take ko?" Ya ɗan matsa kaɗan ya riƙe hannunta "Mammi duk zagaye-zagayen nan na menene? Kin fa san yadda na ɗauki girman alkawari wallahi zan amince, wacece?" Yadda take ta zagayen ne yasa ma yaji yana son sanin wacece haka. "Afeefah ce!" Ɗan shiru yayi yana tunani don sai ya ji kaman ma bai san sunan ba, amma duk inda ya zagaya a kwakwalwarshi mace ɗaya tak ya sani da wannan suna, mace ɗaya da ya sani kuma buduruwar abokinshi ce salim. Da sauri ya kalli Mammin yana girgiza kai "A'a Mammi ki samo wata ba wannan ba" Da zuciya ɗaya yayi maganan kuma kai tsaye. "Ban gane in samo wata ba, Meyasa?" "Mammi ni wannan ta yi min yarinya wlh ba na son hauka da raini, sannan Mammi buduruwar saleem ce fa! Ta ya zan fara zaman aure da ita?" Murmushi Mammi tayi a maganan nashi na farko "Ina saleem ɗin? Ina yana chan yayi aure yana zaune da matar shi? Ko ma bai yi aure ba ba zan amincewa Afeefah ta auri saleem ba ba kuma don shi a karan kanshi ba sai don mahaifiyarshi ba zan so ta koma inda zata sha wahala ba shiyasa na zaɓa mata kai ina da yakinin za ka kula da ita har karshen numfashi" Tayi maganan cikin tabbatarwa, duk ya ɗan ruɗe mata kaman zai yi kuka ya fara magiyar ta chanza wata shi dai wannan yarinya bata mishi ba. "Ba fa zan fasa ba Saraki sai ka bani kwakwarar hujjar da zan gamsu ban da buduruwar saleem, ban da kuma baka sonta itama bata son ka dukkanku za ku koyi son juna idan zama ya haɗa ku, banda kuma tayi yarinya don kaima ka san ba yarinyar bace" Hangota kawai yake a idanunshi yana son tuna menene kuma aibunta wannan idanu farare manya da take zarowa duk sadda yayi magana yake hangowa kawai, da ɗan sauri yace "Mammi baƙa ce!" Dariya Mammi ta fara tana girgiza kai ya kwaɓe fuska shi da gaske yake "Yaushe kuma ka fara zaɓar kala? Kenan ni da babanku bai aureni ba kenan ko kuma da Su Jannah ba za su auru ba" "To ai ku daban ne ita daban Mammi" "Ka san Allah idan ba legit hujja zaka kawo ba, maganan nan babu fashi ka fara shiri... Saboda yanayin jiki na ba za mu ɗauko wani hidima ba ɗaura aure kawai za'a yi ayi walima kowa ya shaida ta tare" Duk yadda ya so ya zamewa Mammi ya kasa, don komai ya ce tana da amsa har aka kira la'asar ya tashi ya tafi, ta bishi da kallo tana murmushi idan ta ga yana hira da ita haka hakan na yi mata matukar daaɗi a rai, ta kan rasa Meyasa baya son Magana alhali ya iya ba bai iya ba, kawai dai ya zauna shiru ya fi mishi ko mahaifin su Jannah da yana raye sai dai ya ji dariyar ta ba zai ji maganan Sarakin nata ba yayi ta tsokanarsu kenan tana shigarwa Sarakin don shi bayan ita wasa da sakin fuskanshi babu mai gani gwara ma saleem da suka shaku sossai shima don salim ɗin ya karanci halayenshi ne tsaff kuma ya iya zama dashi. Tana fata ko ba yanzu ba ya so Afeefah ya sake mata fiye da yadda ita take ganin wannan side ɗin nashi, hannu ta ɗaga tana roƙon Allah ya nuna mata wannan rana da zata miƙa shi ɗakin matarshi. Daga nan ta miƙe ta shige don alwalar la'asar, bata yi ƙasa a gwiwa ba da daren ta sa driver ya kaita gidan ƙanin mahaifinta Uncle Musa dattijo ne sossai shima kuma natsatse mai tarin ilimin boko da arabi yana da zuri'a kuma duk zaman lafiya suke da su Mammi, sossai ta mishi bayanin Afeefah ta kuma roƙi da su je su nema mata aure a wurin dangin mahaifinta don a fita hakkin su, bata so su bada komai amma tana son A karɓi auren Afeefah daga shakikanta. Ya gamsu shima kuma yayi na'am da hakan sun yi hira sossai don tana kwana biyu bata je ba sbd jikinta shi ne ma ya kan zo har gida ya duba ta haka yaranshi da wasu jikokinshi, bata bar gidan ba sai da suka tsayar zai yi tattaki da kanshi da babban danshi su tafi Dutsen-wai su nemi a basu ranar auren daga nan sai a fara shiri. **** Mommy ce kwance a kan gado tsabar damuwa da tunani da ta sakawa kanta ne ya sa jininta hawa sossai, su Samha ke zagaye da ita a yanzu ɗin ma hawaye take zubarwa na tausayin Saleem da damuwar halin da yake ciki wanda ta yarda laifin ta ne amma me yasa su Yaya za su rama alkhairinta da mugunta? Me ta musu da zafi haka? Bata gama tunanin ba Sabrina ta shigo ɗakin ta samu wuri ta zauna "Sannu Hajiya mommy ashe kuma jiki ya ƙi?" Mommy ta danne tace "Eh amma Alhamdulillah" "Toh Allah ya kara sauƙi dama Saleem ne ya aiko ni" Yadda ta kira sunan sai da suka daga kai duk suka kalleta. "Wai cewa yayi ku koma wanchan tsohon gidan na gado ya riga ya tashi 'yan hayan yana son yayi renovating nan, kin ga yanzu mun yi yawa ga iyali zai fara tarawa ga su Gaje gininsun ya tsofe cikin ko wani minti zai iya rufta musu suma dai duk nan za su dawo" Galala suke kallonta da kyar mommy ta iya cewa "Saleem ɗin ne yace haka?" "Ai kin san ban san yan hayan ba bare in tashe su, shine yayi komai kuma ya tabbatar min kar ku wuce yau don gobe masu aikin za su fara zuwa" Wasu irin zafafan hawaye ne suka shiga sulmiyo wa mommy da su Samha, Sameera ce ta iya daurewa ta miƙe tsaye ta fara hada kayan mommyn don ba zasu zauna ba, gwara su tafi ɗin babban matsalar dukkansu babu mai aiki cikinsu karatu suke yi, mommyn sai kallonta take tana jin tururin zafi a zuciyarta tuni Sabrina ta fice, mommy tashi tayi ta fito kai tsaye ta haura saman su ta buga, su Samha duk suka bi bayanta jikinsu a matuƙar sanyaye sai da tayi mintuna biyu kan aka bude saleem ta ƙura wa ido sama da seconds goma kan tace "kai ka ba matarka saƙo ta ba mu?" Kai ya gyaɗa "Duk abinda tace haka ne!" Jiri ne ya kwashe ta ya yunkura zai tare ta ta ture hannunshi ta juya da sauri ta sauƙa su Samha ta cewa su hada kayansu duk suka hada suka fito a motar sadiqa suka zuba duk abubuwan buƙatar su ta ja suka fice daga gidan dukkansu suna kuka, basu sake jin tashin hankali ba sai da suka iso gidan duk 'yan haya sun lalata shi komai dai sai a hankali kuma dakuna biyu ne da parlor sai kitchen duk jiki a sanyaye suka zauna a parlorn mommy na dafe da kanta har lokacin kuka take yi. "Mommy..!" Sameera ta kira sunanta. Sai ta ɗago ta kalleta "Kina jin zafi a ranki ko? Kina jin ciwo da raɗaɗi ko? Kina jin baƙin ciki da tsantsar damuwa da tashin hankali ko?" Mommy tace "Ba sai na faɗa ba Sameera abin da nake ji ba zai misaltu ba ni saleem ya ɗaga daga gidan shi zai dawo da surukanshi? Ni fah? Ko a mafarki ban taɓa zato ko tsammanin saleem zai iya juya min baya a kan mace ba" "Mommy in faɗa miki gaskiya? Laifin ki ne, dukkanmu muna da laifi a abin da ya faru... Mommy kin yi tunanin inda Afeefah ta nufa da muka kore ta? Gwara mu muna da nan kuma ko ba komai muna da junanmu amma ita kaɗai ta fita bata da kowa bata da inda zata je, kin tuna irin wulakancin da muka mata? Ashe alhakin da muka raina zai iya bibiyarmu, kin tsane ta ne saboda saleem yana son ta kina ganin son nan da yake mata zai sa ya bijire miki kika zaɓa mishi wacce kike ganin ke ce da riba sai kuma akasin hakan ya faru. har yanzu kina ganin laifin Yaya da kika mishi dolen karbar wacce bai taba so ba? Kina ganin laifin Yaya da ƙarfi da yaji yana kuka yana komai kika raba shi da Masoyiyar shi? Mommy ina jin zafi ina jin ciwo ina ji a zuciyata cewa duk wannan abinda ya farun alhakin yarinyar nan ne, Allah ya jarabceni da azabar so na ji yadda itama ta ji a sadda muka raba ta da nata savior ɗin, na ji kwatar abinda yaya ya ji a kanta amma muka hadu muka nufeta da sharri har da ƙagen lalata da samari wlh idan ba mu neme ta mun nemi yafiyarta ba to kadan kenan muka fara gani" Dukkansu maganganun sameeran sun shige su barin ma mommy da Samha dake ta kuka, gaskiya Sameera ta faɗa bata kyauta ba kuma duk laifin ta ne da tun farko ta kwaɓe su ba zasu yi ba amma bakin alƙalami ya riga ya bushe sai dai su tari gaba, tana tuna irin abubuwan da suka mata tana tuna irin yadda taje ta haɗa ta da maza don tayi rayuwa saboda kawai an ce ne ita Mayya ce sai ka ce jahilai waenda basu yi karatun islama ba sun ci zarafinta baiwar Allah, sai gashi Allah ya nuna musu ɗan Adam ko ya yake mai daraja ne a gareshi, ya nuna musu ikon shi a kan bayinsa. "A ina za mu sameta mu nemi yafiyarta a ina zan ganta Sameera?" "Wannan sai Allah mommy, yanzu ina so ki daina yiwa yaya kuka mu dukufa Adu'a da sadaka Allah ya karkato da hankalinshi mommy adu'ar ki karɓaɓɓiya ce a gareshi ke kika ɓata ke ya kamata ki dukufa ki gyara" Ta gamsu sossai kuma ta fahimci karatun duniyar, ta fahimci ayar da Allah ya nuna a kanta don haka gwagwalanta ta cire ta ba sadiqa akan su je su sayar su musu sayayyan duk abinda za su buƙata haka suka fice kasuwa suka bar su su biyu da Samha da har lokacin jikinta kaman an zuba mata ƙanƙara. 🖤Gureenjoh🖤 HAIHUWA DA HANJI (A True life story) Fatima Muhammad Gurin (Gureenjoh) Wattpad-Gureenjo6763 Arewabooks-Gureenjoh ADABI WRITERS ASSOCIATION *FREE BOOK* *31* A hankali kwanaki ke ja har ranar da Uncle Musa ya yanke da za su tafi Dutsen-wai su samu kawu, shi da yaranshi manya biyu sai Driver suka ɗauki hanyar, tafiyan awanni kaɗan ya sada su da kauyen, kusan abin da ya faru da 'yan uwan Sulaiman hakan ce ta faru amma dayake ya riga ya sani suma kuma sun sani so basu wani damu ba. A kofar gidan Labaran suka yi parking motar su biyu suka fito suka bar uncle ɗin cikin mota, gidan da rabin shi a zube a ƙasa suka ɗan zubawa idanu suna mamakin me ya kawo Rayyan har nan neman aure? Daga ka ga gidan zaka san suna fama da masifar talauci, buhuhuna ne da suka zama jajazir aka kare ɓangare guda na gidan dashi, ga yara nan dukunkun rabin su tsirara suna ta wasa a kofar gidan, daga gefe wasu matasa ne suna shaye-shayensu ko a jikinsu, ɗayan na shirin turawa a kira musu mai gidan sai ga kawu Labaran ya fito a zuburen shi ganin mota ya sa ya taka birki "Lafiya?" "Ƙalau sai Alheri, Malam Labaran muke nema" Kanshi ya nuna "Ga ni" Girgiza kai babban da sunanshi Mansur yayi wani abu sai bakauye Dukda wasu kauyukan mutanen cikinshi akwai kara da girmama baƙo haka kuma mutane suna suka tara, amma babu gaisuwa babu komai bare iso ko ruwa kawai a yi abinda ake so. "Mun zo ne akan maganar 'yar wajenka Afeefah" Uncle Sanusi ya faɗa, tun ma kafin ya gama kaiwa aya Kawu ya katse shi "Wace Afeefah? Ai mu bamu da Afeefah a zuri'ar mu kap" Uncle Mansur yace "Afeefah 'yar wajen ƙaninka?" "Ah Annoba zaka ce sai na fi ganewa, ai na jima da sallamar wa duniya ita ko a chan ne tayi muku wani abin ba wurina za ku zo ba ita za ku kama babu ruwan Labaran Ah to" "Malam ka natsu mana ka ji bayanin da muke tafe dashi" Uncle Mansur ya faɗa da ɗan zafi don yana da faɗa shi, Buɗe kofan da Mahaifinsu yayi ya fito ne ya sa suka yi shiru, uncle Musa ya miƙa mishi hannu suka gaisa ya ce "Ba wani abu bane ya kawo mu illa nemawa jikana, ɗan wajen su auren 'yarka Afeefah, mun zo ne da batun na gani ina so idan babu damuwa zaka iya ba mu rana sai mu zo a ɗaura aure" "aure??" Ya faɗa yana sake kallonsu Dukda sun yi zubin masu hankali kuma kaman suna da kuɗi amma wani gida ne zasu yadda dansu ya auri Afeefah? Kila dai basu san wace ita ba, zayyano musu wace ita da mutanen da ta kashe ya shiga yi har abinda ya sa ta bar garin "Duk mun san da hakan" Uncle Sanusi ya faɗa. "Kuma kuka yarda ɗan ku ya aureta?" "Eh a haka yake sonta, bama buƙatar komai daga gareka ita ɗin ma ba sai ta dawo nan ba auren kawai muke so ka bamu da kanka kuma mutanen garin nan su shida zaman aure zata cigaba da yi ba dadiro ba kaman yadda kuke ta faɗa" Numfashi ya sauƙe ai tunda babu abinda suke so shikenan kila ma suma manyan mayun ne don waenda basu ji tsoro ba bayan jin labarinta ai basu da maraba da mayun, kuɗi har dubu hamsin suka bashi a cewar na gani ina so ne. Ya hangame baki yana kallon uban kuɗin kaman faɗa ya karɓa yace tunda sune zasu zo su gaya mishi kawai randa suke so a daura, suna ta mamaki shi ba ruwanshi da bincike ko wani abu tunda ya ga kudi kawai ya ruɗe, suka tsayar da nan da wata guda a haka suka yi komai daga tsaye suka shiga mota suka juya suna mamakin ƙarantar mutumin. A chan wurin kawu kuwa kaman zai kifa ya shiga gidan "Asabe, larai ku fito ku ji abin mamaki wai na kwance ya faɗi" Duk waje suka yo larai ta kasa shiru "Wannan uban kudin fa malam daga ina haka?" "Nima duk kaina ya kulle, wasu ne suka zo yanzu a mota wai sun zo neman auren Afeefah wannan kudin na gani ina so ne suka bayar" "Afeefah dai???? A mota?? Wannan uban kudin kawai na na gani ina so ne? Kuma ka amince musu??" Duk a jere suka jero tambayoyin cike da tashin hankalin hassada. "Toh ko ban basu ba ai zasu iya auren tunda ba gabanmu take ba tunda suka ba da wannan a na gani ina so ki yi lissafin nawa zasu bayar sadaki?" "Amma malam Afeefah annoba Mayyar taya zata yi aure ta bar yaranmu zaune? A dandi fa take basu sani bane?" "Sai da na basu labarinta tsaff kuma sun ce sun ji sun gani" Wani irin abu ne ya taso ya tsayawa inna larai a makogoro Ah ba zai yiwu ba, sam Afeefah bata chanchanci auren mai kuɗi ba dole ta san yadda zata yi zama bai ganta ba. Ko ta kan bayanin da kawun ke tayi bata bi ba shi lissafin zuwan kuɗin shi yake don ya ce sai ya bi Afeefar ya ga inda zata zauna in gidan kudi ne yayi ta zuwa ana bashi kasonshi ai ta zauna gidanshi sama da shekaru goma yana ciyar da ita a banza. Inna larai gyale ta saɓa ta fita afujajan ko auren ya lalace ko kuma ya dawo kan daya daga cikin 'ya'yanta ba zai yiwu tana ji tana gani Afeefah ta yi aure inda zata je ta huta ba su suna nan suna cin wuya, har ita a wa? Daji sossai ta shiga sau ɗaya ta taɓa rako wata kawarta wurin bokan don bata taɓa zuwa ba amma ganin aikinshi yayi a kan kawarta ya sa ta gamsu zai iya wargaza auren Afeefah ya dawo dashi kan 'yarta, ɓacewa tayi tayi ta zagaye a garin neman inda zata kulla sharrin ta maciji ya sare ta, wani irin ihu take da kururuwa tana neman taimako Allah ya taimaketa akwai wasu mutane a gona suka zo suka fara taimakonta kan aka ɗauko ta mutu kwaikwai rai kwaikwai aka dawo da ita cikin dutsen wai, abu kaman wasa kafa ya fara zama wani abu daban kaman ba macijin gaske ba don duk maganin da ake yi na macizai an yi mata sai zabura take ga zazzabi tayi sharkar da gumi tana surutai... **** Afeefah na zaune tana azkar na bayan Magrib Abeeha ta shigo tana shigowa ta rangada guda "Ahayye matar babban yaya bi'izinillahi nan da wata guda za mu sha shagali" Gaban Afeefah ne yayi wani irin faɗuwa, kenan wata daya suka saka auren? Jikinta yayi wani irin sanyi ta fara jin hawaye na zuba mata dukda ta amince har ranta da auren sai dai tana jin wani irin ciwo a ƙasan ranta na auren wanda baya sonta bai ma dauketa mace ba, kila ma ko sunanta bai sani ba don bata taɓa ji ya ambata ba, Abeeha ce ta tsuguna tana tsokanarta har ta fara kukan auren kenan? Da kyar tayi shiru. Bayan isha Mammi ta aiko aka ƙirata bayani ta mata akan kwanakin da aka sa auren, bata ce komai ba Mammi ta ce zata iya tafiya a Washegarin aka fara zuwa yi mata gyaran jiki don mammi sossai ta tashi tsaye Dukda ciwo dake nukurkusarta amma auren ɗan farinta babu batun zama, shi dai kam ma a satin aka tura shi wani assignment Zamfara ya wuce kuma zai yi akallah sati uku. **** Ta ɓangaren su mommy fa rayuwar ya juye musu, a hankali suka fara fahimtar abin da rayuwa ya kunsa barin ma da ta mayar da sunna Tv da kuma Africa tv3 abin sauraro, suna takure sai dai basu rasa ci da sha ba kuma duka yaran suna zuwa makarantar su sai dai hankalinsu ba'a kwance yake ba, ga ayyukan su da suka manta yadda ake su wanki, guga, shara wanke wanke da girki duk su suke yi idan basa nan suna school haka mommyn ce ke yi dole, ko wani dare karfe uku baccinta ya ƙare don ciwo ne sossai a ranta na abin da aka yi wa saleem, tana roƙon mishi waraka kuma tana roƙon Allah kar ya kama shi da laifi don ba laifinshi bane nata ne. Yau da ta ji tana matuƙar kewanshi ta tura Sameera da Samha gidan akan su duba shi, ko da suka je kaman baƙi haka suka tsaya jikin kofan suna knocking kusan mintuna biyar tukuna Gaje ta zo ta buɗe ganinsu ya sa tayi murmushi "Ah ashe su Sameera ne sannunku da zuwa bismillah" Sai suka ji wani iri a gidansu ne ake musu iso? Shiga suka yi suka samu Yaya zaune cikin kujera relaxed irin gidan shin nan, zama suka yi suka gaishe shi ya amsa kan Samha tace "Wurin Yaya ne muka zo yana nan?" "Eh yana nan bari na dubo Sabrina ta turo muku shi. Talatuwa..! Talatuwa...!! Kawo musu ruwa" Su dai banda ikon Allah babu abinda suke gani wai in faɗa ya fi karfinka sai ka mayar da shi wasa ba kuma baki sai kunne murmushin dole kawai suke yi har Talatuwa ta fito, da tausayi take kallon su amma ya zata yi dole ta cigaba da aiki da mutanen da suke gidan in tana bukatar abin rufa wa kai asiri, ruwan ta kawo musu ta gaishe su suka amsa a sanyaye. Sun fi mintuna talatin kan ya fito ya zauna yana kallon su itama Sabrina ta zauna gefenshi don su Gajen duk sun tashi sun yi wuraren da nan ne ɗakunan Mommy da nasu suke a baya, gaisheshi suka yi ya amsa "Lafiya?" Ya tambaya sai Samha ta fara zubar da hawaye, wai yaya saleem ne ya zama musu baƙo? Yaya saleem dai da yake matuƙar kaunarsu ne wannan zaune? "Rashin kunyar taku ne kuka zo har nan ku cigaba ko? Duk wanda kuka dinga yi mata a baya bai ishe ku ba?" Shiru suka yi don basu san me suka yi ba wani irin tsawa ya daka musu "Ba Za ku gaishe ta ba??" A ɗan razane suka shiga gaisheta tayi murmushi tana amsawa har da tambayar su mommy na lafiya? Suka amsa da lafiya lau. "Me kuke so? Ba na ce zan neme ku ba?" Ya faɗa har yanzu babu walwala a fuskarshi "Dama mommy ce tace mu zo mu duba kana lafiya?" "Jinjiri ne ni? Ko idan banda lafiya ku nake jira ku kaini asibiti?" Shiru suka yi sai Sabrina ce tace "My S ka daina fushi ai ba laifi bane don sun ji lafiyarka, ku je ku ce mata yana lafiya yana miƙa saƙon gaisuwa kuma bai manta da ita ba zai zo idan ya shirya shikenan?" Sameera ta miƙe ta kama hannun Samha "Za ta ji, sai anjima" Ta jata suka fice sai kuka samhar ke yi har suka shiga napep hannun Sameera ta rike "Sameera har da laifina a mayar da yaya saleem haka, duk ni ce da ban kiraku ɗakin Afeefah ba da bamu san suna soyayya har mu raba su mommy ta aura mishi wannan fitsararriyar mai ido a tsakar ka ba" "Samha ki daina wannan kukan, komai ya wuce dukkanmu muna da laifi... Ki yi shiru bana so mu je wurin Mommy kina cigaba da wannan kukan kar hankalinta ya sake tashi, Yaya Adu'a yake bukata ba kuka ba" Dukda itama hawaye take sharewa lallai ta yarda duk soyayyar Uwa ga ɗa tana iya zama mummunar kaddararshi ko da sanin ta ko akasin hakan, mommy ta zamewa salim mummunar kaddara sai dai Allah ya bashi ikon hayewa ya bashi ƙwarin zuciyar ɗauka kar ya halaka a haka. **** A sati uku da suka biyo baya idan ka ga Afeefah za ka rantse da Allah ba itan ba ce, Caramel skin ɗinta wani irin daukar ido da sheki yake, tayi wani irin kyau har ta gaji, ba gyaran jiki kaɗai ake yi mata ba sessions ne daban daban a satukan ga karatu, ana koya mata dressing irin na wayyayyun matan aure, ana koya mata girke girke na zamani da bata kware ba ana kuma koyar da ita rayuwar auren da ma auren karan kanshi haɗe da dabarun zama da miji, ta ɗan rame saboda stress amma ta wani irin cikowa tayi kyau masha Allah, ba kananun kudi Mammi ke bararwa ba Dukda ba buki za su yi ba sam. Ko da su Umman Sulaiman suka ji labari su ma ba'a bar su a baya ba, Baaba jummai ta kan zo ta yini bata shawarari kuma tsaff take ɗauka wasu dai sai dai tayi murmushi don ta san ba dai Rayyan za ta yiwa ba don wani abin bata tunanin har abada ma zata yi amfani da shawarar, mixed emotions take ji akan auren. Wai ita ce Afeefah za ta yi aure? Ita da ta fara sallamar da zancen aure a rayuwarta saboda mummunar Taɓonta, ko da a da ta yi tunanin auren tayi tunanin aure zai zo mata a kaskance cikin rashin galihu da gata, auren da zata iya zuwa ta cigaba da shan wahala kaman yadda ta faro a rayuwarta sai gashi ta samu gatan da bata taɓa tunani ba, gatan da ko iyayenta suna raye karshen abin da za su yi mata kenan, ta kan raba dare tana kuka tana miƙa godiyar ta ga Allah tana kuma roƙon shi da kar ya nuna mata ranar da za tayiwa waennan bayin Allahn butulci. Yau Asabar da wuri ta tashi don sun yi class da mai koya mata girki, gasashen kifi suka yi talapia ya ji onion sauce sai irish da aka gasa aka yi ganishing a gefen kifin, a gefe wani hot beef stir fry jollof Rice ne, a dining suka shirya don ita da Abeeha suna ci Mammi ce dai ba zata ci ba, bayan sun gama taje tayi wanka yadda aka nuna mata sabon method na yi har da dauraye jiki da ruwan turare ta fito tana zuba uban kamshi, gaban wardrobe ta tsaya tana tunanin kayan da zata saka, a hankali ta zaro wani dogon riga mai yanayi da silk material ta zura yayi mata kyau sossai don A line ne rigar bai kai ƙasa sosai ba kuma ƙasan ba a zagaye ba ana iya ganin idanun sawunta, hula mai butterfly a gaban Goshi ta saka ta ɗan tsaya gaban madubi sai taga kaman kayan ya mata yawa bata fita classy ba, komawa tayi ta nemi belt ta ɗaura a daidai cikinta sai ya bata wani kyaun na musamman murmushi ta saki ta ɗauki wayanta ta fito, daidai Abeeha ma ta fito daga nata ɗakin. "Ku ne kyau amare" Ta tsokani Afeefar da kullum aikinta kenan, murmushi Afeefah tayi don tun tana rigima har ta gaji ta shiga kyale Abeehar. "Wlh Afeefah kina da kyau, kaman fa wata model haka kika fita, duk kayan da zaki sa yanzu kin san irin adon da zaki musu su fita daban" Suna shiga cikin parlorn suke zancen, Afeefah na cewa "Addah Abee ai ina ga zan saka fashion design cikin mafarkaina don gaskiya abin na burgeni bana rabo da kallon fashion show" "Toh ke madam komai ma kina so? Ke fa kika ce business woman kike son zama na inna naha don kina son yin kuɗi" Ta faɗa da dariya. "Ai duk mace tana bukatar waennan a gani na fa, kin ga girki ya zama favorite thing ɗina saboda wajibi ne a gidan aure, dressing ma wajibi ne in kana so ka burge masoyinka duk ba laifi bane business kuma shine asalin abin da nake so, ina so nayi kuɗi na samu na kashewa marayu da bayin Allah, ina so nayi kudi na tallafi rayuwar yaran da suke wahala a duk sadda suka rasa iyaye, gidauniyoyi nake mafarkin buɗewa na wayar da kan mata akan mecece rayuwa da kuma yakar jahilci a yankunanmu" Abeeha na dariya take cewa "Su burge masoyi, a'a ka ga Masoyiyar Ya Ra..." Katse wa maganar yayi suka tsaya chak idanunsu a kan Rayyan dake zaune dining yana karyawa hankali kwance, kuma tsaf ya ji su don daskare wa da suka yi ya sa ya ɗago firgitattun idanunshi ya zuba musu yana aika musu da kallo mai kama da gargaɗi.... 🖤Gureenjoh🖤 HAIHUWA DA HANJI (A True life story) Fatima Muhammad Gurin (Gureenjoh) Wattpad-Gureenjo6763 Arewabooks-Gureenjoh ADABI WRITERS ASSOCIATION *FREE BOOK* *32* Idanun ya ɗan tsayar a kan Abeeha kan yayi baya da su kaman zai ɗauke sai ya sauƙe a kanta ya ɗan tsayar kan ya janye ya mayar kan abincin shi ya cigaba da ci in his majestic way. Wani irin bugawa zuciyarta ke yi fiye da misali, ko da wasa bata ji Mammi na maganar zuwanshi ba daga ita har Abeeha kasa gaba suka yi kuma sun kasa baya, ita dai Afeefah tsabar bugun zuciya har idanunta sun tara kwallah kiris take jira ta sako su, a tare suka juya za su bar wurin suka ji muryarshi ya ce "Ku zo nan!" Wani irin tsalle zuciyar dake bugawa yayi, ita dai bata san Meyasa bata iya controlling heartbreat ɗinta ba in dai akan magananshi ko kallonshi ne ta ajiye akan tsananin tsoron shi da take ji ne ya janyo hakan, Dukda bai taɓa dukan ta ba amma ya sha yi mata faɗa, faɗan ma babu kaman na ranar da ta fara ɗora idanunta a kanshi a rayuwarta. Kaman waenda kwai ya fashe musu suka dawo, Abeeha da ta san halinshi ba lallai ma ya kara magana ba ta ja kujera ta nunawa Afeefah kujeran da idanu, kaman ba zata zauna ba sai kuma ta zauna Abeehar ma ta ja wani ta zauna ta ɗauki plate a hankali ta yi serving ɗinsu Rice ɗin daban daban Allah ma ya sa shinkafar da tsokar nama suka yi da babu protein za su ci don shi zallar kifi da irish ɗin yake ci. Abeeha ta fara ci a hankali kan ta buɗe baki tace "Sannu da dawowa Yaya" Kai ya ɗan gyaɗa har lokacin bai ɗago ba, ita dai Afeefah ko spoon ɗin bata ɗauka ba gashi tana tsoron magana, kuma kar bata yi ba ya zama laifi da kyar ta ce a rarrabe "S..sannu da d..dawowa" Yadda tayi maganan ya sa ya ɗago slowly ya kalleta kan ya mayar da kanshi yana kai fork na karshe baki bayan ya haɗiye ya ɗauki ruwa daga fari kal ɗin glass cup dake gefenshi ya sha kan ya miƙe ya bar wurin, a tare suka sauke ajiyar zuciya Afeefah tace "Adda Abee Meyasa da ya dawo da mu kika sa muka zauna?" Tayi murmushi tana cin shinkafar tace "Har yanzu baki san Yaya Rayyan ba, ai ya tsani saboda shi ka ƙi yin abinda ke gaban ka yanzu da za mu tafi bayan ya kiramu ya kuma san me za mu yi anan muddin muka tafi haka zai titseyemu ya tsare gida ya ce sai mun faɗa mishi dodo ne shi da muke avoiding ɗinshi..." "Shi dai komai kayi baka burgeshi?" "Aikam bana tunanin akwai abinda yake burgeshi muddin ba abinda ya shafi Mammi bane" Ajiye hirar shi suka fi suka cigaba da cin abinci don hanyar lafiya a bita da shekara dazu sun tsira gaba basu san me zai faru ba. Bayan sun gama wurin Mammi suka yi suka samu ma tana waya ne da wata cousin ɗinta akan boxes da ake haɗa mata na auren, ita dai Afeefah a kunyace ta zauna don yanzu sai take jin kunyar Mammin na rufeta, bayan Mammin ta gama waya ta dube ta "Afeefah yaushe ne kuke gama exams ne? Bana so kina yawo cikin rana ana wannan gyaran jikin" "Mammi wednesday za mu ƙare" Ta mayar mata da amsa. "Da sauƙi, saturday ne ɗaurin auren Abeeha ya zancen telan?" Sai da gaban Afeefah ya faɗi ita ta kasa sabo da zancen auren sam, ji take kaman ana daddaureta ne in aka yi maganar sai ta ga kaman ba gaske ba ita ce zata yi aure, auren ma Rayyan za ta aura? Ya subhallah wani chill take ji yana running over her spine. "Mammi kin san telan Jannah ne zan ƙirata na ji ko ya gama haɗawa ko ni sai in je in karɓo" Hira suka cigaba da yi akan bikin da za'a yi shi ne a yini guda, ɗaurin aure, yini, walima da miƙa amarya ɗaki in ji mutanen garinmu suka ce Jollof, ba ana yinshi bane saboda talauci ko wani abin, ana yin hakan ne saboda sauƙaka zirga-zirga expecially a irin situation na Mammi da bata bukatar stress ko kadan. Ranar Juma'a ana yi mata lalle sai ga su Fa'iza da fauziyya har da Ummusalma matar Sulaiman da ta sake da ita sossai a yanzu, ga Abeeha da Jannah sai suka zama kaman bridemaids suka cike ɗakin da hirarraki ana yi ana dariya, Mammi kuwa sai sawa take ana turo musu abubuwan taɓawa sossai hakan yayiwa Afeefah daaɗi sai take jin nishadi a ranta na taruwansu ko ba komai Allah ya haɗa ta da tarin mutanen kirki, wani irin kyau lallen nata yayi baƙi da ja ya karɓi hannu da kafafunta duk suma 'yan matan sun yi. Mammi ma tayi ja a yatsun hannu. Sai dare suka tafi har Jannah akan sai gobe da sassafe za su dawo. Rana bata ƙarya sai dai uwar ɗiya ta ji kunya, yau aka wayi garin Asabar kuma a yau ne ake shirin ƙulla wani babban al'amari mai tarin nauyi tsakanin Afeefah da Rayyan, da misalin karfe takwas ya shigo ɗakin Mammin don ta kalli kayan da ita ta bashi ya saka a ranar don rana ce ta musamman a gareta da ma shi baki ɗaya. Ɗan uban sun Men lace ne fari kal mai shegen tsada ƴar ciki da babban riga ya wani zauna mishi sak kaman don shi aka halicci yadin, hula da takalminshi bakake ne haka agogo tsadadde dake ɗaure tsintsiyar hannunshi zuwa azurfa mai baƙin dutse da ke ƴar yatsar shi, fasalta irin fita a angon da yayi ma ɓata lokaci ne sai kamshi kam kaman an yi barin turare, fuskar Mammi ya zubawa ido kawai don bai taɓa ganinta cikin nishadin da ya ganta a ranar ba sai ya ji wani abu mai sanyi na sauƙa cikin zuciyarshi, matsowa tayi ta kama hannunshi tana murmushi tace "Za ka tafi a saurayi ka dawo matsayin magidanci Saraki, ba zan ce komai ba illah Allah ubangiji ya tsare muku hanya daga zuwanku har dawowanku" Yayi murmushi ya juya zai fita tace "Saraki...!" Ya waigo ta ɗauko turarenta ta sake fesa mishi ya fita ranshi fess Dukda wani abu da yake ta ji na tsungulinshi akan auren. Ga dumbin mamakin shi yana fita ya tarar da motoci sun fi sha biyar dauke da tarin ma'aikatan asibiti da ma 'yan uwanshi sojoji, a hankali ya juya ya kalli Sulaiman da ke mishi murmushi sai yaji wani abu na mishi yawo a jiki, bai taba zaton za'a mishi irin wannan karan ba duba da gaisuwa ce kawai ke hada shi da kowa, wani iri yake ji a sadda ya shiga gaban motan Sulaiman suka fara barin unguwar babu saleem, ya nemi saleem a waya har ya gaji baya samunshi ko da ya dawo gidan ya je mai gadi ya tambaya ya tabbatar mishi sun yi tafiya da madam, ya tambayi su mommy yace basa nan suma. Ko jiya sai da ya koma amma bai same shi ba akan basu dawo ba bai ji daaɗi ba sam da hakan ta kasance. Bai gama shan mamaki ba sai da ya kalli tarin dangin Mammi, iyalai da jikokin uncle ɗinta motoci kusan nawa har da abokanan arziki don a matsayin auren jikan Uncle ɗin za'a yi, kan su tafi Mammi ta roƙi uncle Musa akan duk runtsi a dawo da sadakin Afeefah wanda Saraki zai bayar in ya so ko wani abu ne a bashi daban amma sadaki na Afeefah ne. Mutanen Dutsen-wai suna zaune kawai suka fara ganin lafiyayyu kuma tsararrun motoci suna shigowa one after the other, babban masallacin garin da bashi da wani girma sai haraba suka yi wa tsinke tuni dama Uncle Mansur ya aiko da masu canopies an kafa dayawa a harabar don masallacin ba zai ɗauki mutanen ba, an shimfida carpets-carpets anan suka yi masauki, Kawu an nemo na ƙasan akwati don maƙon shi ma bai barshi yayi sabon ɗinki cikin dubu hamsin din chan ba bai tashi jin kunya ba sai da ya ga mutanen alfarmar da suka taru a wurin, kowa mamaki yake yara sai leke suke wasu matan ma na maƙale saman katangu ana kallon ikon Allah, kowa Allah Allah yake a ce wannan shine mijin Afeefah Annoba su kare mishi kallo... Fara haramar ɗaurin aure ake, a hankali Rayyan ya kalli Sulaiman "Nawa ake bayarwa?" Sulaiman ya ɗan juya hannu alamar mene kenan? "Sadakin?" "Duk abinda kake dashi hawa hawa ne amma last da na duba a masallaci ƙarancin sadaki yana dubu ɗari da tamanin da uku ne" A lokacin aka fara ambatan sunayensu a hankali ya karkata ya zaro bandir ɗin dubu-dubu guda biyar ya miƙawa Uncle Sanusi aka miƙawa liman an ɗaura auren Afeefah Kamal da Rayyan Moh'd Khamis akan sadaki naira Dubu ɗari biyar lakadan ba ajalan ba, wani irin yanayi ne yake ratsa shi da ya kasa fahimta, idanunshi da suka sauya ya runtse yana ji ana ta rabon goro da dabino da sweets. Sai hannu ake bashi ana mishi murna da kyar yake iya kawo murmushi fuskarshi don yanayin da yake ji baya misaltuwa mishi, kawu sai kallonshi yake baki galala yana ayyana lallai wannan zai iya zama maye tunda gashinan irin mazan da yake kallone idan yara suna kallon India, a fina-finan ma wannan ko ya aka yi kuɗinshi daban ne, limami ne yake rike da kuɗin sadakin kawu yaje ya fara kokarin karɓa sai uncle Musa yayi interrupting ɗinsu "Kun dai san sadaki hakkin mallakar matar ce ko?" Limamin ya gyaɗa kai "Toh zan tafi da wannan tunda ita yarinyar na gabana zan bata" Yana kai nan ya nuna Mansur shi kuwa ya karɓi kudin gabaɗaya wani irin kullutun bakin ciki ne ya tasowa kawun har wuya, uncle Musa ya murmusa ya fiddo dubu hamsin ya ba kawun Dukda haka bai huce ba sai kumburi yake, anan aka yi reception 'yan kauyen sun ga abinci da kaji iya gani, yana ta mamakin ya aka yi Mammi ta shirya waennan abubuwan with her condition, duk kauyen babu gidan da ba'a ci shinkafa da kajin auren Afeefah ba don enough aka yi shi. Karfe goma sha ɗaya suka fara barin garin, kawu ya tafi zai shiga mota Uncle Musa ya janyo shi "Malam Labaran na ga kana kokarin shiga mota?" "Eh wai dama in je ne in kalli inda 'yar tawa za ta zauna" "Ah ai ba'a yi haka ba, ba yanzu ba zaka bari sai ta kwana biyu da kaina zan zo in kai ka yanzu ka ga mutanen da ka tara dole ka tsaya ka ga sun tafi cikin salama" Yana maganan ne yana tuna zancen Mammi da tace duk rintsi kar su dawo da kowa, tana so ta dasa musu wani bakin ciki ne a rai gashi dai wacce suka kora sun haɗa ta da ƙaddarar ta rabonta shine ya kawo ta har cikin Kaduna, sannan gashi sun gani kuma sun shaida a yanzu ta shallake wa tunanin su kuma babu yadda za su yi babu abin da suka iya. Kwalelen biri da hantar kura. Shi dai bai gamsu ba amma haka uncle Mansur yayi ta mishi zaƙin baki har motocin suka watse illa Sulaiman da Rayyan wanda yake jingine jikin mota ya harde hannayenshi a kirji yana mamakin ikon Allah wai yau shi ne da aure. Ko sha'awar kallon kawun baya yi don ko da kawun ya zo yana washe mishi baki tattare girarshi yayi ya haɗe fuskarshi ta koma ainihin shi mai tarin kwarjini dole kawun ya kyale shi. Su ne karshen barin garin sai masu canopies, sai cece kuce ake to Annobar ya saki Afeefah ne ko an mata maganin mayun ne? Kap kauyen babu yarinyar da aka ɗaura mata aure kwatankwacin na Afeefah, sadakinta kaɗai yayi sadakin mata ashirin a kauyen kaf... Inna Larai na zaune da suntumemen kafa da kullum kara hauhawa yake tana jin komai tana hawayen bakin ciki, inna Asabe ma sai uhmm uhmm take tayi abin duniya ya taru ya masu yawa barin ma da aka aiko kulolin abinci wai na gidan kawun, ko da Afeefah ke mata abincin sayarwa wannan yayi jarinsu sau goma don daga ganin shinkafar ka san ba na yara bane ga kaji baja baja. Suna gani Afeefah ta haye? Garin yaya duk basu sani ba. Ni kam na ce Allah take dashi. Ko da suka iso Kaduna shi kadai ya nufi babban parlorn akwai mutane ciki sossai don yan uwa Mammi duk suna nan ga su Umma duk sun zo yara ana ta ciye ciye ana wasa, kai tsaye karamin parlorn Mammi ya leƙa sai ya ga wata cousin ɗinta tace mishi "Tana sashen ka Rayyan" Bai amsa ba don duk ana ta ango ango kanshi kasa da kyar yake dan murmusawa don kanshi sara mishi yake. A parlorn shi kuwa ya samu Mammin da wasu, tsayuwa yayi kawai yana kallonta ta ci wanka cikin leshi blue doguwar riga ta ɗora gyalen da ya shiga da leshin a kanta da aka yi wa dauri mai kyau, daga wuyanta kunnenta zuwa hannayenta da yan yatsunta gwalagwalai ne da suka kawata adonta ta mishi kyau ainun har bai san ya fadada murmushin shi ba ya shigo ciki. Ta tako a hankali ta kama hannunshi sai hawaye suka shiga zubo mata "Alhamdulillah! Alhamdulillah!! Alhamdulillah!!! Allah na gode maka da ka nuna min wannan rana, Allah na gode kwarai da ka ba ni lafiyar kasancewa da ɗana a rana mafi muhimmanci cikin rayuwarshi, Allah ka dube su ka basu zaman lafiya Allah ka sanya musu tausayi, jin kai, bege da kaunar junansu ka bashi ikon bata kariya da sauƙe duk wani hakki nashi na aure... Rayyan..." Sai ta kasa magana sai hawaye, kaman zai yi kukan shima yana jin adu'o'in nata har a cikin zuciyarshi ya sa hannu yana dauke mata hawaye, jan shi tayi suka zauna ta zaro wayanta ta kira Abeeha "Ku zo da ita" Daga haka ta kashe. A gefen Mammin ya zauna yana gyara mata gyalenta nan masu hoto suka shiga aikinsu, sossai suke yin kyau don shine yake ba ta kulawa bayan ya gama gyara mata gyalen ya sake share mata fuska kan ya kalleta yana murmushi duk ana ɗaukar su, suka kalli cameran suka murmusa a tare ba karamin kyau suka yi ba, zai yi magana suka yi sallama suka shigo ganin murmushin Mammi yayi yawa ya sa ya kai idanunshi inda take kallo. Afeefah ce ke tahowa a hankali kaman wacce ke tafiya a kan ƙaya, tayi masifar kyau cikin wani exlusive luxery lace da aka yi wa ɗinki na amare, ko ina na jikinta a rufe ne ruf banda hannu da fuskarta makeup da aka mata ya matuƙar amsarta ko don shine karo na farko a rayuwarta ne bata sani ba, amma kam tayi kyau Tabarakallah. Mammi ta miƙe ta tarbota "Masha Allah, Tabarakallah ɗiyata you made a beautiful bride" Shi kam kallon seconds biyu yayi mata ya janye idanun har suka zo suka zauna Mammi tana tsakiya Afeefah na gefenta na hagu yana zaune a gefenta na dama, idanunshi ya ɗan tsayar akan yatsun Afeefar da suka yi kyau ainun har yanzu mamaki yake, Mammi ce ta kama hannun shi ta kamo na Afeefah ta haɗe a tare suka ɗago sai zuruf idanunsu suka faɗa cikin na juna, idanunta da suka sake haske suka yi mai saboda kwallin da aka saka mata ya tsayar da kwayar nashi a kai, ba zata iya jurar kallon ba sai ta duƙar da kanta daidai Mammi ta ɗora nata hannun a kan nasu camera man yayi musu magana suka kalleshi aka shiga ɗaukar hotuna. Ko da za'a musu su biyu Mammi bata tafi ba don ta san in ta bar wurin shima sai ya bari, ta miƙe ta mishi umarnin komawa mazauninta ya koma ɗin amma har lokacin da space tsakanin shi da Afeefah mai hoton ya kalleta yace "Amarya ki ɗan matsa kadan sai ki sa kan ki akan kafadarshi" Irin bugawar da zuciyarta ke yi tunani take kila saura kiris ya fashe ta mutu, kamshinshi presence dinshi a kusa kusa da ita haka sai ya nemi ruda ta, yana so ya tashi don ya gaji hakan ya sa ya ɗan matsa kaɗan Jannah da duk tsoronta ta zo ta kama hannun su ta haɗe sai suka kalli juna don duk sadda jikinsu ya haɗu su suka san abinda suke ji, kallon ya ba da wani ma'ana na daban nan aka shiga daukar hotuna. Sossai yake a takure na tsaye aka ce shine last Mammi dai bata yi magana ba amma idanunta ne ya hana shi barin wurin wallahi. Bayanta ya koma, ya matso sossai har tana jin kirjinshi na taɓa bayan nata babu zato ta ji hannunayenshi duk biyu ya zagaye cikinta, a ɗan razane ta ɗora nata biyu a kan nashi "Kin natsu ko sai na karyaki biyu? Baki san mutum ya gaji bane??" Da ɗan faɗa yayi maganan a kausashe amma wanda suke tare za su dauka wani abin arzikin yake rada mata aka daddauka ya zame ya bar wurin su ma suka fice. An yi yini an ci an sha an yi hidima har la'asar kan aka sake wanka aka fito harabar gidan walima, amarya na sanye da wani tsadaddiyar Abaya da yanayinshi kaɗai ya bayyana tsadar shi canopies da kujeru aka shirya sossai aka yi walima aka ci aka sha kan mutane suka fara watsewa don bayan isha aunties ɗin su Jannah za su kaita part dinshi dake cikin gidan, Mammi bata mishi maganan wani gida ba saboda ta sani ne ba zai taɓa tafiya ya kyaleta a gidan ba, kuma parts dake gidan kenan don a tsare aka yi ginin Allah ma ya sa dakuna biyu ne a nashi part ɗin da kitchen da store sai parlor da dining section kaman flat ne mai zaman kanshi. Aiko kan bayan isha mutane kadan ne a gidan masu aiki sai aikin tattare gidan suke, Afeefah tayi sallah aka shirya ta again cikin atampha aka ɗora mata lafaya aka miƙa ta wurin Mammi, sossai ta yi mata nasiha tana hawaye itama kuka take don bata da bakin godiya ga Mammi, ta yi mata abubuwan da godiya sun yi kadan ta cika mata burinta na ganin ta auru, ta rungumeta ta zame mata uwa da uba ta bata duk wani gata da take tunanin ta rasa to da me zata saka mata in ba da zama lafiya da kuma zuciya ɗaya jal da ɗan ta mafi soyuwa a gareta ba? Sossai take kuka tana tuna mamanta da Aunty zee ina ma Aunty zee na nan ta ga wai Afeefah ce a ɗakin miji? A haka aka kaita ɗakinta da Adu'a a Bakinta. Mammi waya ta ɗaga ta kira shi, ba'a yi mintuna biyu ba ya shigo sanye da kananun kaya ash har da hoodie don zazzabi yake ji tsabar hayaniyar da yake ji ya mishi yawa ya saukar mishi da ciwon kai sossai. "RAYYAN...." 🖤Gureenjoh🖤 HAIHUWA DA HANJI (A True life story) Fatima Muhammad Gurin (Gureenjoh) Wattpad-Gureenjo6763 Arewabooks-Gureenjoh ADABI WRITERS ASSOCIATION *FREE BOOK* *33* "Rayyan a yau Allah ya nufa ka sake samun wani nauyi a kanka bayan nawa da na ƙannenka, na san ba wai ka ganta bane ka ji kana so har aka yi muku aure Allah SWT ka ba zaɓi shi kuma ya zaɓa maka abinda ya fi dacewa da kai da kuma rayuwarka, idan har ka ci amanar ta ko ka ha'inceta ba ita ka yi wa ba Allahn da ya baka shi ka yi wa, kar ka kalleta domin ni, kar ka so ta domin ni, kar ka yi mata wani abu na alfarma domin ni duk abin da zaka yi mata ka yi saboda Allah, idan ka so ta ka so ta saboda Allah don Allah ba don ni ba ka ba marar ɗa kunya. Ka zame mata gatan da ta rasa, ka zama uwa, uba kuma jigo a rayuwarta, ka zama majingina a gareta ka tallafi rayuwarta daga cikin duhuwa zuwa haske madawwami" A hankali ya ɗan ɗora kanshi a gefen kafaɗarta sai ta ji hucin zafin jikinshi na sauƙa Mata, hannunta ya kama "Mammi in shaa Allahu zan yi amfani da duk abin da kika ce" Daga haka bai sake magana ba, ta san a takure yake ta kuma san akwai abinda ke cinshi a rai a yanzu haka wanda bata tantama shi ya haddasa mishi zazzabi kuma muddin ya cigaba a haka ba zai yi bacci ba amma sam ba zata tambaya ba, ba za ta matsa mishi ba. "Ka tashi ka sha magani Saraki" Ta faɗa, da kyar ya buɗe lumsassun idanunshi da suka rine ainun ya miƙe zaune, karbar pills ɗin yayi ya sha wanda ta haɗa da panadol a hankali ya kalli time karfe tara ne da wani abin, Miƙewa yayi yana mayar da hannayenshi cikin aljihun hoodien jikinshi cike da dauriya yace "Sai da safe" "Allah ya baka lafiya" Ya amsa da Amin kan ta mishi sai da safe ya fice da kallo ta bishi ta san sai a hankali zai saba da wannan sabuwar rayuwar kuma, ta san sai Afeefah tayi haƙuri ta kara juriya kafin ta samu yadda take so da shi matsalar kawai ya kasance ta shiga ranshi murmushi ta ɗan saki kan ta sha nata maganin itama ta shiga don kwanciya saboda kowa ya tafi baƙi kam duk babu kowa. Wani iri yake ji a haka ya kutsa kanshi cikin parlorn bakinshi ɗauke da sallamar da iya shi kaɗai ya san yayi kayanshi, taku biyar yayi ya samu kujera ya zauna yana dafe kanshi da kaman zai rabe gida biyu, numfashi ne yake mishi wahalar fita kuma ya san yanayinshi ne da tunanin da ya saka a ranshi, wani irin zafi yake ji kaman ana ɗora mishi wuta a kan zuciyarshi ina ma da zai iya da kuka zai yi da ihu zai yi ta yi sai ya samu salamar abin da yake ji a ranshi, zamewa yayi ƙasa kan carpet ya ɗora kanshi a kujeran yana rike zuciyarshi ya jima sossai cikin wannan yanayi sai da ya ɗan samu relief ya miƙe ya nufi ɗakinshi kai tsaye, ruwa ya sha har gora uku kan ya shiga zame kayan jikinshi daga wurin yana nufan bayi, ruwan sanyi ya sakarwa kanshi yana yamutsa gashin kan nashi a lokaci ɗaya yana dan buga glass ɗin wurin wankan da hannunshi. Sai da yaji zai iya faɗuwa idan bai bar wurin ba ya fito ɗaure da towel ya hau gadon ya kwanta ko ruwan jikinshi bai tsaya tsantsanewa ba ya ja bargon ya rufe har kanshi ba wai don zai yi baccin ba don ko ya rufe ido abin da ya tsana yake kallo. Ita kam Afeefah dama ta san ba zuwa zai yi ba, bayan kowa ya tafi ta miƙe tana kallon ɗakin har lokacin zuciyarta ke maimaita mata wai ita ce fa matar aure, yanzu ita ta tashi daga buduruwa matar auren ma wai matar Rayyan, Allah buwayi gagara misali Allah mai yadda ya so a lokacin da ya so, a hankali take bin ɗakin da kallo ya ji kaya iya kaya yayi kyau fiye da misali gashi wadatacce don za ta iya komai free ciki yana da girma, akwatunan da aka jera mata ta bi da kallo guda goma sha biyu wai akwatunan aurenta ne, ita dake da kayan da basu wuci biyar ba ita dake fama da allura da zare a kullum tana facin kaya ita dai Afeefah Annoba kuma Mayya, sai hawaye suka fara sintiri a idanunta tana jin karin imani tana jin wani irin yarda da ubangijinta. A haka ta shiga bayin shima ta ƙare mishi kallo komai na 'yan gayu, bata yi wanka ba don sai da tayi wanka ta saka kaya aka kawo ta karamin akwatin da Abeeha tace mata kayan bacci ne ciki ta buɗe ta duba silk riga da wando cream Color yana da adon Black lace daga kirji da kuma ƙasan kafafun wandon ta saka, kamshinta da kamshin ɗakin har ya so yayi mata yawa ga sanyin Acn dake busawa kashe wutan tayi ta hau gado ta kwanta tana sake jin salama a ranta sam bata wani sa damuwar rashin ganin Sarakin ba don ta riga ta sakawa kanta haƙuri da juriya har Allah ya kawo karshen komai Dukda bata san yaushe ba bata san ko karshen zai zo ba amma she have her trust in Allah zai mata komai ba sai ta damu kanta ba Adu'a ne babba kuma zata cigaba. Washegari da safe bayan tayi sallah ta ɗan koma bacci, ƙarfe tara ta farka ta sauƙa daga gadon da kaman kar ta tashi tsabar daadinshi da take ji ta wuce bayi ta yi wanka ta fito ta fara neman kaya cikin sababbin dinkunan da telan Jannah ya chanchada mata, wani atampha doguwar riga A shape ta fitar ta shirya ciki tayi kyau sossai ta feshe jikinta da turarukanta sababbin waenda kamshin suka yi mata ta kafa ɗauri, bata sa kwalli ba sai ta saka lipstick kawai accesories da tayi anfani na silver sai suka ƙara haskata tayi kyau ainun gidan ba baƙonta bane amma sai ta fara tunanin ta saka gyale ne ko kar ta saka? Tsoro take kar ta fita su haɗu don yanzu ba kaman da bane da ba lallai ma su hadu ba in ba wurin Mammi ba, a hankali dai ta sa hannu ta buɗe kofan ɗakin ta sanyo kai cikin parlorn, ko taku biyu bata yi ba idanunta suka sauƙa kanshi a farko ta tsorata sai kuma ta fahimci kaman bashi da lafiya ne don ga matar da take matsayin likitarshi zaune a kujeran dake fuskantar shi, yayi relaxing sanye da wasu blue pjamas riga da wando complete, kafafunshi babu takalmi suna lume cikin tattausan carpet ɗin dake shimfide parlorn, fuskarshi yayi ja sossai haka gashin kanshi a hautsine. Wani iri taji a ranta sai taji tausayin shi na bin jikinta kaman ruwa, ta riga ta san dalilin da ka iya kawo mishi ciwon a hankali ta shigo cikin parlorn Likitar na kallonta ta saki murmushi itama ta mayar mata a hankali ta ɗan duƙa ta gaisheta ta amsa da kulawa tana tambayarta Ya Rayyan da jiki? Ita dai ta amsa da da sauƙi amma bata ma san bashi da lafiyan ba sai yanzu. A hankali ta kalleshi idanunshi na a lumshe har lokacin, matar ta miƙe "Allah ya baka lafiya zan zo gobe da safe, please make sure ka ci abinci ka sha waennan pills ɗin" Ta karashe tana ajiye mishi wasu pink pills a roba. Sai a lokacin ya ɗan buɗe ido "Thank you" Tayi murmushi ta yiwa Afeefah sallama ta fice. Sai aka bar su su biyu a parlorn, yatsina fuska yake don kamshinta har kanshi yake ji ba tun yanzu ya fara ji ba tun ranar da suka same shi a dining da Abeeha ya iya bambance nata kamshin da na Abeeha, yanzu ma gashi ta zo ta tsaya mishi sai hawa kanshi yake tsaki ya ɗan ja ya buɗe ido sai karap suka hada idanu don kallonshi dama take tana tunanin ta inda zata fara gaishe shi ganin ya kalleta sai tayi saurin cewa "Ina..kwana!" Ya yunkura ya miƙe zaune da kyau, bata yi zaton zai amsa ba sai jin deep and calm voice ɗin shi da bai yi matcing da situation da yake ciki ba ya ce "Good Morning!" Daga haka ya miƙe ya wuce ta ya shige ɗakinshi, ta sauke numfashin tsoro tana nufan kofa saboda knocking da ake, masu aiki ne rike da baskets na abinci kai tsaye suka jere mata su a dining suna gaisawa don sun saba da juna dama, plates, cups da spoons taje ta ɗauko ta zo ta ƙarasa haɗa dining ɗin amma bata sani ba ta kirashi ne ko ta kyale shi, ta san ba zai so shisshigi ba in ta dameshi ya iya karyata don ya sha ambata kalan ya zo ya faru ta shiga uku, abincinta ta zuba ta ci har ta gama karyawa bai fito ba don haka tayi sashen Mammi don ta duba ta. A zaune ta sameta ta gama karyawa tana shan magani tana ganinta fuskarta ya washe da fara'a "Ɗiyata ni da nace yau za ki huta sossai sai ga ki da sassafe? Sannu da zuwa" Yadda take mata sai ya saka kunya kamata kaman wacce ta fito daga wani unguwar, a ƙasa ta duƙa ta gaisheta tana mata ya jiki. "Alhamdulillah dawo nan gefena Afeefah, ina shi Sarakin?" Wani kunyar ne ya sake lullubeta ta kasa magana Mammi tayi dariya kawai ta janyo wayanta ta kirashi "Jiya ya tafi anan ban gamsu da yanayinshi ba, kun gaisa da safen nan?" Kai ta gyaɗa "Eh na fito na same su da likitan shi suna magana" "kin ga ko, sai in rasa Meyasa yake ajiye damuwar da baya bayyanawa yanzu baya so in sani ne ya ƙi zuwa nan tun sassafe na kira ban same shi ba je ki ce ya zo" Gabanta ne ya faɗi rassss, ta ya zata fara kiranshi? A hankali ta miƙe ta fice zuciyarta na racing har ta shiga parlorn inda Allah ya taimaketa ma ta samu yana parlor a zaune kan dining yana karyawa wayanshi na a speaker alamu waya yake, a gefenshi ta ja ta tsaya sai ta ji Muryar dake tashi kaman ta san Muryar kuka me Muryar take har tana shidewa a hankali take cewa "Ya Rayyan bakin cikin Ya Saleem zai kashe mana Mommy, duk abubuwan da ya dinga yi a baya mai sauƙi ne yanzu ya kore mu ya saka surakanshi a gidan, bai damu da mun ci ko bamu ci ba, mun yi karatu ko ba mu yi ba muna lafiya ko babu tun muna zuba ido yanzu wata kenan da ko mun je gidan ba'a bari mu shiga, ga mommy kwance a asibiti saboda damuwa da hawan jini...!" Dukda maganan da take yi ɗin ya shige shi sossai, damuwa ya nuna a kan fuskarshi sai dai bai tanka ba har ta gama ta cigaba da kukan. "A wani asibiti take?" Ya jefa maganan a hankali "Tana 44 ne, anan muke da file" Kai ya gyaɗa kan ya katse wayan, Afeefah dake tsaye jikinta ne yayi wani irin sanyi a hankali zuciyarta ke motsawa da wani irin yanayin damuwa ba dai saleem da ta sani ake magana akai ba? Amma ai wannan Muryar ta Sadiqa ce, saleem ne har ya kori mahaifiyarshi a gidanshi? Ko jikinta duka kunnuwa ne ba zata yarda yana cikin hankalinshi yayi hakan ba, Wani irin tashin hankali ne ya zo mata har ta kasa boyewa ta manta waye a gabanta tace "Yaya Saleem ne cikin wannan hali? Shi ne ya kori mahaifiyarshi da kanshi? Su Samha ne ke cikin irin wannan damu..." Haɗa idanu da suka yi ya sa maganar ta katsewa idanunta har sun cika da kwalla suna shirin zubowa, gani irin kallon da ya mata ya sa ta saukar da idanun ƙasa, ajiye spoon ɗin hannunshi yayi ya zari wayan bai miƙe ba yana nuna ta da wayan ya ce "Kika kuskura kika sake hawaye ɗaya ya zubo miki a kan fuska za ki gane ba ki da wayo...!" Mukut haka ta haɗiye kukan zuciyarta na cigaba da racing cikin mixed feeling ga idanun da ya zuba mata yana jira ya ga zata yi kukan ne ko ba zata yi ba ga damuwar halin da ta ji wai saleem na ciki. "Mam..mi na ƙiran ka" Ta faɗa a ɗan tsorace. Kwafa yayi ya miƙe ya fice daga wurin da sauri ta dafa dining ɗin tana jan kujera ta zauna.... 🖤Gureenjoh🖤 HAIHUWA DA HANJI (A True life story) Fatima Muhammad Gurin (Gureenjoh) Wattpad-Gureenjo6763 Arewabooks-Gureenjoh ADABI WRITERS ASSOCIATION *FREE BOOK* *34* *Don Allah readers ina ɗan so ne in ja hankalinmu a kan wani abu da na fahimta, zan ɗan yi magana ne da miyaun marubuta. A duk sadda marubuci ke rubutu ba duba iya zallar nishadantarwa yake ba ko da kuwa littafin akan nishadi ne, ba son rai ake dubawa ba saboda ba shi ne ake son isarwa ba, duk sadda marubuci ya ɗora alkaminshi a kan Littafi tunanin farko da zai fara shine me ya kamata na isar? Shin wani saƙo ne nake da shi a cikin labarin nan da zan ba al'umma kuma su amfana da shi? Kar mu raja'a ga iya fannin nishaɗi ko soyayya don rayuwa bai taɓa tafiya babu ƙalubale ba... Don haka don Girman Allah mu daure muna karatu ta fuskar ɗaukar darasi don akwai darusa masu yawa da marubuci kan jefa a cikin kowani labari wanda ba sai an fito fili an ce yi kaza kar ka yi kaza ba mu dinga kokari muna fahimtar hakan saboda mu marubuta mu samu ladar ku👏🙏* **** Da kyar ta iya danne kukan da ke taso mata, tsoron Allah na ƙara rufeta tana tuna irin iko da isan mommy akan saleem ashe har za'a iya samu macen da za ta raba wannan iko da isar cikin lokaci kankani haka? Miƙewa tayi ta nufi sashen Mammi, ba za ta zuba ido rayuwar saleem ya cigaba da tafiya a haka ba don salim ya cika mutum cikakke ɗari bisa ɗari ya taimaketa a sadda bata da mai taimako bayan Allah, shi ne namiji na farko da ya fara nuna mata so tsakani da Allah ba tare da kyama ko tsoron tabbatuwar zancen al'umma a kanta ba, ya hana hawayenta zuba ya kuma ƙarfafa mata gwiwa akan jajircewa da haƙuri da rayuwa, ta san babu abin da zai saka saleem saɓawa mahaifiyarshi don ya san darajar ta fiye da kowa face sharrin asiri. Abin da ya sake bata mamaki ya ɗaure mata kai shine ta yaya wacce mommyn ta yarda da ita har ta aura mata saleem ba tare da yana so ba ta zama sanadiyar rabuwarta da ɗanta? Sam bata kawo cewa ko alhakinta bane saboda ta san ita ɗin ba dolen su ba ce da su taimaketa da kar su taimaketa duk wannan tsakaninsu da ubangiji ne yo waenda suka zama dolen nata ma basu mata ba sai bare ne za su mata? Ta saka a ranta son zuciyar mommy ne ya janyo mata wannan wahala da suke ciki, tayi negleting duty ɗinta a matsayin uwa tana ganin dabararta shi zai sa 'ya'yanta su cigaba da zama ƙarƙashin ikon ta alhali 'ya'ya ba ababen iko da gadara bane ta manta Allah ne ke da dukkan iko akan bayinsa kuma shi ne ya san abin da yake fili da na ɓoye. Ko da ta isa wurin Mammi bata samu Rayyan ba, zama tayi cike da damuwa tace "Mammi Yaya saleem na cikin masifa" Ta ƙarasa idanunta na cika da kwallah, Mammin ma ta fahimce damuwar Afeefar don Saraki ya sanar da ita komai kuma tausayin Saleem ɗin duk ya rufeta itama. "Yanzu Saraki ya gama sanar mini, nayi mamakin yadda aka dau lokaci bai zo ba har ma aka yi auren Saraki saleem ba ya a kusa da shi ashe abin da ke faruwa kenan, laifin mahaifiyarshi ne Allah ya sa wannan abu da ya faru ya zame mata Aya ya sa ta hankalta" Kai Afeefah ta gyaɗa tana amsawa da "Ameen ya rabbi, Mammi ina so in taimaki Saleem Dukda ban san me Ya Saraki zai yi ba amma ina so in ba saleem gudummawa kaman yadda ya ba ni a sadda na rasa madafa don Allah ki taimakeni akan hakan" Ta ƙarasa a karye. "Me kike tunani Afeefah?" Mammi tayi tambayar cike da kulawa. "Mammi ina so ki yi convincing Ya Saraki akan za ki dinga bashi magani yana saka saleem sha ni kuma zan dinga haɗa zobo ko wani kalar drink da ayoyin da mafificin annabin mu annabi Muhammad (SAW) Yayi mana umarnin amfani da shi don karya sihiri, ko da kurba bibbiyu zai yi Allah zai ba mu nasara kuma ina so zan yi wani abu na sadaka da tawassilin Allah ya dube shi ya dawo dashi hayyacinshi kar mahaifiyarshi ta mutu da damuwarshi" Sossai Mammi ta yabawa hankalin Afeefah ta kara jin kuma tabbas bata yi wa Rayyan zaɓen tumun dare ba, ta gamsu kuma da shawarar don haka ta tabbatar mata zata bata duk wani taimako da take so. Afeefah ta ji daaɗi ta koma ɗaki ta fara neman takardar ta da tayi rubutu akan hakan a sadda malaminsu na islamiyyat ke koyar da su, ta kuwa samu bayan dogon bincike Adu'a kawai take a ranta Allah ya taimaketa. **** Rayyan na fita Asibitin ya wuce kai tsaye ya samu kuwa mommyn na jin jiki yaran sai kuka suke yi, har ranshi tausayinsu yake ji kuma yana jin su ne tamkar su Abeeha, shi karan kanshi a yanzu ya gamsu cewa asiri ne ke dawainiya da abokin shi in ba haka ba ko mahaukaci ai ya san girma da darajar uwa. "Kukan nan me zai yi mata? Ko ba ku san Adu'a shi ne makamin ko wani mumini ba? Ko kukan lafiya zai bata?" Da ɗan faɗa yayi maganan don sun cika mishi kunne, duk shiru suka yi don sun san shi baya ɗaukan nonsense da likitan da ya duba ta yaje yayi magana don anan ɗin ma yana da office kuma yana aiki da nan ɗin Dukda ya fi zama Capital. Daga nan ya shiga ya duba ta tana bacci ya dawo ya kallesu yana so yayi magana da hankalinsu zai kwanta bai iya ba sai cewa yayi "Komai zai wuce in shaa Allah" Daga haka ya zaro kuɗi mai yawa ya basu kana ya fice, yana shiga mota Mammi ta ƙira shi a waya. "Saraki idan ka samu Saleem ko da a waya ne kar ka yi mishi magana da tashin hankali, ka bi shi da lalama kuma kar ka tsananta magana akan mahaifiyarshi da 'yan uwanshi ka nuna baka damu ba don kar matar tashi tayi yunkurin shiga tsakaninku don akwai abinda nake so kullum ka tabbatar kana bashi yana sha, shi ramin ƙarya a koyaushe ƙurarre ne zai wuce ne kaman ba'a yi ba" Ya gamsu kuma ya san Mammi wani abin zata sama mishi na karya sihiri ya ji daaɗi don bai san ya zai yi ba, ya tabbatar saleem a gidan ba zasu barshi yayi komai na malamai ba bare yace zai kaishi wurin wani malami. A kan ibada da azkar ne zai tsaya sossai ya ga saleem ɗin ya koma yi don tun da chan ɗin shi saleem ba mai wasa da ibada bane kai duk iya ibadarka idan Allah ya nufa kamun asiri na cikin jarabawarka dole sai ya kama ka sai dai ka samu sassauci saboda ka riga ka yi tawasilli ubangiji shine mai yin komai. Kai tsaye gidan Saleem ya je Allah ya bashi sa'a ya dawo don yana horn aka buɗe mai gate a mota ya tsaya ya shiga kiran Layin saleem ɗin ringing na karshe aka sada shi dashi, amsa sallamar kawai yayi ya ce "Ina waje" Yana kai nan ya yanke wayan kusan mintuna uku sai ga saleem ɗin ya fito, ido kawai Rayyan ya kura mishi don kaman ba shi ba ya ɗan yi duhu kuma ya tara gashi sannan fuskarshi babu walwala haka ya iso ya buɗe gefen zaman banza ya shiga ya zauna. "Ya kake?" Saleem ɗin ya tambayi Rayyan yana kallonshi. "Lafiya ƙalau, ka yi wuyar gani." Murmushi yayi wani dry smile da babu annuri ciki "An tura ni Lagos ne wani aiki shine muka tafi da madame fa, inda nake kuma babu wani service na kirki" Kai Rayyan ya gyaɗa. "No wonder, ya kowa da kowa?" "Lafiya ƙalau" "mu shiga mana in gaishe da mommy kwana biyu ban leƙa ta ba" Saleem ya ɗan yi shiru don wlh ya manta da ya tura su chan gidan. "Mommy bata nan sun koma tsohon gidan mu" "Amma me yasa? Ina haya kuka saka a chan?" Ya ɗan yi shiru "Eh, nan ɗin ya ɗan takura mu ne ga iyayen Sabrina sun dawo shiyasa nace su koma chan" Kai kawai Rayyan ya girgiza duk ranar da Allah ya bashi macen da zata raba shi da Mammi bai san irin hukuncin da zai mata ba don idan bai kasheta har lahira ba sai ya nakasata yadda ba zata taɓa amfani ba har abada. "Ya Mammi da jiki?" Saleem ya katse mishi tunanin da yake yi "Tana ta faɗan kwana biyu baka shigo ba ai, ni kam saleem in tambayeka mana?" Kai yaa gyaɗa mishi "Ya tsakaninka da ubangijinka?" Ya ɗan yi shiru kan ya kalli Rayyan ɗin "ban gane tambayar ba, ina sallah biyar a rana yadda aka umurci kowani musulmi" "na sani, ina magana ne akan nafilfili musamman na dare da na sanka da shi da azumin nafila, yau ka ma yi azkar na safe?" Numfashi saleem ya ɗan sauƙe kaman abin na damun shi "A gaskiya na manta rabon da in yi wani azumi da Sallar nafila, azkar ne nake dan yi watarana wani sa'in wani abu ya taso ko bacci ya hana ni amma zan yi kokarin ganin na gyara" "Don Allah saleem ka gyara, da karatun alqur'ani kar ka manta ko da baka yi a fili ko baka nuna kana yi ba idan ka ji ƙuncin zuciya ka dinga ambaton Allah zai yaye maka ka ji?" Ya ƙarasa da tausayin abokin nashi, kai ya gyaɗa. "Ka shiga ciki" Rayyan ya faɗa don ganin Sabreenar na tsaye tana kallonsu, ba don tsoronta bane baya so ta fahimci ya san matsalar saleem din kuma baya so ta tambayi saleem ɗin abinda ya wakana tsakaninsu don irin su akwai wayo idan baka iya kama ɓarawo ba aka ce sai ɓarawo ya kama ka. "Gobe zan zo in gaida Mammi" Kai ya gyaɗa "Sai ka zo" Daga haka ya fice shi kuma ya ja motan ya bar gidan. **** Afeefah yinin gabaɗaya bata zauna ba, musamman Mammi ta ba da aka yi mata sayyayar kayan zobo don ta san saleem na son abin, ta dafa shi ta tace bayan ta gama yi mishi haɗi ta zauna ta yadda idan tana karatun numfashinta zai dinga sauƙa ciki ta fara karanto Ayatushifa Suratul tauba aya ta goma sha huɗu 14. Suratul Yunus aya ta hamsin da bakwai 57. Suratul Isra'i Aya ta tamanin da biyu 82. Suratul nahl aya ta sittin da tara 69. Suratul shu'ara aya ta saba'in da takwas har zuwa na tamanin da biyu 78-82. Suratul fusilat aya ta arba'in da huɗu 44. Ta Yi su ne kafa bakwai bakwai, ta yi su da tawassilin cewa Allah zai karɓa har cikin zuciyarta babu kokonto don ba'a yi wa Allah kokonto ta yarda da cewa muddin ya yi amfani da wannan ayoyin na tsawon kwana bakwai duk abin da ke jikinshi sai ya kau. Ba sai a zobo ba ko a cikin ruwan miya ko a cikin ruwan tuwo kai duk abu da mutum zai iya ci muddin aka yi ayoyin nan kafa uku uku ko kafa bakwai bakwai da yardar Allah ko niyyan sihirin ne aka yi maka ba zai kama ka ba bare wanda ke cikin jikinka. A gefe akwai ganyen magarya guda bakwai busassu ta cika farin bokiti surr da kyakyawar ruwa shima ta zauna yi mishi nashi a yayin da Abeeha ke tayata dura zobon a goruna don a sa a frigde. A cikin wannan bokiti mai dauke da magaryan ta shiga karata ayoyin kaman haka: Suratul Fatiha. Ayatul kursiyu. Suratul A'araf aya ta ɗari da shida zuwa ɗari da ashirin da biyu 106-122. Suratul Yunus aya ta saba'in da tara zuwa ta tamanin da biyu 79-82. Suratul kafirun kafa ɗaya. Falak da Nas ƙafa uku uku. Sai ta karanta wannan Adu'a: 'Allahumma rabannas azhabal ba'as washfi antas shafi la shifa'un illa shifa'uka shifa'un la yugadiru saƙaman' kafa uku. Sai ta rufe da 'Bismillahi Urkika min kulli shai'in yu'uzika wa min sharri kulli nafsin Allahu yashfika Bismillahi urkika' shima kafa uku. Hawaye ne ya sauƙo mata bayan ta gama tsaf, ta sa hannu ta share tana Miƙewa tsaye tayi yakini akwai waraka cikin alqur'ani, ta yi yakinin saleem baya bukatar wani boka ko malami da waennan kaɗai Allah zai isar mishi. Sossai Mammi ta jinjina mata don bata bar sashen Mammin ba sai bayan isha, zobon duk a fridge na sashen suka shirya wanda ya kai gora hamsin ta ajiye ruwan ma lungun kujaran da Mammi ke zama a rufe. Sallama tayi wa Mammin zata fita Mammi tace "Ki bi sai ki ɗauka muku dinner ɗin ku daga kitchen na san Saraki yana chan yana jira don tun ɗazu ya yi min sallama" Da Toh ta amsa kan ta fice Mammi ta bita da kallo tana murmushi. A basket yanzu ma ta samu an shirya musu komai da komai ta ɗauka ta nufi sashen, ita dai wannan yanayi da take shiga ta rasa shi don tana tura kofan kamshinshi da ya cika parlorn ya sanar da ita yana ciki kaman kuwa ta chanka daidai don yana zaune kan kujeran dining gefenshi energy drink ne da yake kurba a hankali yana dannan waya fuskan nan babu ɗigon fara'a. Ajiye basket ɗin tayi tana tsoron yin magana ta yi laifi sai ta fara cire kwanukan tana shirya su a kan dining ɗin, ta tafi ta samo cutlaries da plates ta fito da su taje ta ƙaro ruwa da drinks ta kawo ta fara kokarin ajiyewa a lokacin ya ajiye wayanshi ya ɗaga ido ya kalleta sai ta nemi ruɗe wa garin ajiye ruwan goran sai ya faɗi ya Buge cup ɗinshi na energy drink da ta samu a wurin ya ɓare kan wayanshi... Wani irin zaro ido tayi ta zari wayan ta fara gogewa da hijabin jikinta tana furta "Innalillahi..." *Ban yi alkawarin na dare ba amma in har na samu dama za ku ji ni* 🖤Gureenjoh🖤 HAIHUWA DA HANJI (A True life story) Fatima Muhammad Gurin (Gureenjoh) Wattpad-Gureenjo6763 Arewabooks-Gureenjoh ADABI WRITERS ASSOCIATION *FREE BOOK* *Ɗazu na ɗan leƙa online na ga yadda ake cigiyata har gabana ya faɗi na zaci laifi na aikata wai sai na ga ashe Haihuwa da hanji ake nema ido rufe😅 Za ku dinga haƙuri da ni Weekdays gaskiya don Sai yamma nake samun lokaci ko kuma dare, weekend da kuke samu raɓa raɓa ma saboda babu inda nake zuwa ne kuma ba ni da aikin komai, and ban da saka tsammanin pages biyu a weekdays ba zai haɗu ba, don Allah a rage ambaton Gureenjoh razana nake🤣🤣* *35* Baya baya yayi ya jingina da kujerar tare da relaxing, idanunshi har lokacin zube a kanta yana aikin kallon yadda ta ruɗe sai haƙuri take bashi tana share wayan da hijab ɗinta, he is surprise a lokaci daya kuma he's amuse bai taɓa ganin halittar dake tsoron shi irin ta ba, shi ba dogon magana yake mata ba shi ba dukan ta ya taɓa yi ba amma yadda take yi akan wayan sai ya ga kaman cewa yayi zai sa bindiga ya harbe ta. A hankali ya miƙa tattausan hannunshi ya ɗora a kan nata da ke riƙe da wayan, abin da taji shi ya sakata natsuwar dole ta ɗago ido ta kalleshi suka haɗa idanu, for some seconds ya janye idanunshi ya zare wayan ba tare da ya ce komai ba. Ita har ga Allah tana mamakin shegen miskilancinshi ayi mutum babu magana ai sai yayi ciwon baki, ganin bai ce mata komai ba sai ma kokarin saka abincin yake tayi saurin ɗaukan spoon ta shiga serving ɗin shi bayan ta tura mai ta juya za ta bar wurin ta ji ya ce "Ina za ki je?" Juyowa tayi ta kalleshi kaman ba shi yayi maganan ba hasali ma abincin shi yake ci hankali kwance, ganin tsayuwar ba zai mata ba sai ta nufi kujeran dake nesa dashi ta zauna ta ɗan saka abincin kadan ta shiga ci a hankali. Bai fi mintuna ashirin ba ya miƙe ya bar dining ɗin ta bi shi da kallo har ya shige ɗakinshi. Washegari kuwa da Mammi ta faɗa mata saleem zai zo har gidan ta shiga kitchen ta musu girki ta sake yin tofin a ruwan abincin da ta shirya musu, a dining ta jera musu ta wuce ɗakin Mammi tana shiga bata zauna ba yana shigowa, a ƙasa ta zauna wurin kafafun Mammin shi kuma ya zauna daga gefenta Mammi ta amsa gaisuwar da ya fara yi mata ta ɗora da "Ya jiki?" "Alhamdulillah Mammi, ya naki?" Ta amsa cikin kulawa. "Afeefah kawowa mijinki ruwa mana" Wani irin dukanta kalmar yayi a hankali ta ɗan kalleshi shima ita ya kalla jin wani mijinki da Mammi ta faɗa ya janye ido, ta miƙe ta isa fridge ta ɗauko zobon nan da Cup ta kawo mishi tana ajiyewa ya furta "Thanks" Yana ɗan lumshe ido saboda kamshinta da ya shige shi, yana mamakin kalar turaren da take amfani dashi ko yaya ta matso kusa dashi sai yayi perceiving smell din, tsiririn tsaki ya ja. Ta juya zata fita Mammi ta tsayar da ita "Ina kuma zaki je Afeefah ba kin zo taya ni hira bane?" Dukkansu basu yi tsammani ba suka ji muryarshi yana cewa "Dodonta ya shigo dole ta fita." Calmly yayi maganan, ta ɗan wara idanunta bata ce komai ba sai da Mammi ta ɗan yi dariya ta yi rau da fuska a ɗan karye tace "Mammi akwai abin da na manta ne ban yi ba a kitchen shiyasa zan fita fa" Ya ɗago cup na zobon yana sha suka haɗa idanu da sauri ta fice, ya juya ya kalli Mammi "wannan yarinyar ta cika tsoro da yin abu a zabure, ko ina haɗiye mutane ne?" Shi dai da gaskiyar shi yayi maganan yana mamaki kuma. Dariya sossai Mammi tayi "Ka haɗiye mutane ai babu zaman lafiya kawai yadda kake ɗaure fuskar ne yayi yawa Saraki, ya kamata ka sakar mata tunda matarka ce" Bai tanka ba chan ya ɗaga cup na zobon "Yayi daaɗi." "matarka ce tayi!" Ya kalli Mammi yana maimaita matarka a zuciyarshi Mammi har ta haddace kalmar, zai yi magana ƙira ya shigo wayanshi saleem ne, Miƙewa kawai yayi ya fice. Chan sai gasu sun shigo babban parlorn, Mammi ta fito suka gaisa tana ta mishi magana baya shigowa yanzu ya dube ta yana murmushi mai nauyi yake furta "In shaa Allah zan ke zuwa Mammi" "yauwa gwara kam ka zo Saleem, idan ba damuwa ma ina so in roƙi alfarmarka" A kunyace yace "Mammi kun wuce alfarma ai a wurin mu sai dai umurni" "Yauwa toh na gode da wannan matsayi, idan har ba zaka takura ba ina so in dinga ganinka kullum for seven days akwai maganin kariya da Saraki ke sha ina so ku sha tare duk aikin naku ɗaya Fatan mu dai Allah ya kare mana ku ya sa ku gama lafiya" Suka amsa da Ameen, cike da biyayya da yake da shi tun chan yace "Na gode sossai Mammi kuma in shaa Allah zan ke shigowa har kwana bakwan" "yauwa Allah ya muku albarka, ku isa ga abinci chan an shirya muku a dining" Tana kai nan ta miƙe ta koma sashenta, hira suke ɗan yi kaɗan kaɗan a hankali ya ɗan lumshe ido ya buɗe kan chak ya miƙe yana furta wa saleem "Ina zuwa!" Corridor da zai kai ka side ɗinshi daga nan babban parlorn yayi aiko a gab wurin fitowa parlorn suka yi karab da ita har tana Buge mishi ƙirji, baya baya tayi tana ɗagowa suka haɗa idanu sanye take da wani riga da skirt na lace da bai wani kamata ba amma yayi masifar amsarta kasancewar shi Red colour tayi ɗaurin ture ka ga tsiya, ɗan kunne ne kawai a kunnenta bata saka sarƙa ba sai wuyan nata ya fita fresh yana ɗaukar idanu, ga mamakin ta mugun kallo ta ga yana mata sai ta sake shan jinin jikinta. "Ina kike tunanin zuwa?" Tambayar sai ya sakata cikin duhu dama ina take zuwa a gidan da ya wuce wurin Mammi ko Abeeha. "Ina magana kin yi min banza? Na fara wasa dake ne?" Da faɗa yayi maganan sai ta matsa baya idanunta na cika da kwallah tace "wurin Mammi za ni" "Daga yanzu har nan da kwanaki bakwai ko da wasa bayan gaisuwan safe da za ki je yi wa Mammi ki bari mu yi ido huɗu dake a main parlor sai ranki yayi mummunan ɓaci, wuce ki bani wuri" Hawayen da take ta riƙe wa na tsoron ne ya zubo mata da sauri ta juya ta koma, bai bar wurin ba sai da ya ga ta ɓace ya ja tsaki mai ƙarfi ya juya ya koma parlorn, inda ya tashi ya zauna yana sake jan tsaki. "Lafiya kam?" "Ƙalau, mu je mu yi lunch azahar ya kusa" Miƙewa saleem yayi suka isa dining ɗin Rayyan yayi serving ɗinsu suka zauna suna ci saleem sai yabon girkin yake har suka gama suna ɗan hira tsakaninsu daga nan suka shiga wurin Mammi ta haɗa su da zobon Dukda sun sha a dining bayan ta basu maganin a cup masu kyau duk su biyu suka sha saleem yayi mata sallama suka fito tsakar gidan. Suna shirin fita masallaci Motar Abeeha ya shigo gidan tayi parking tana saukowa fuskarta a ɗan washe ta gaishe su, duk suka amsa saleem na tambayarta school ta amsa da Alhamdulillah daga nan ta shigo ciki su kuma suka fice daga gidan, sai bayan sun yi sallah ya zo ya ɗauki motar shi ya wuce gida, shima Rayyan mota ya ɗauka ya tafi duba Mommy ya samu da sauƙi sossai ma akan idanunshi aka bata sallama shi ya biya duk bills ɗin kasancewar akwai mota bai kaisu gida ba sai kwantar wa mommy hankali yayi suka tafi shima ya nufi gidan. Ita kam Afeefah ɗakinta ta koma ta zauna akan kujerar mirror tana kallon kanta, a hankali ta sa hannu ta dafa saitin zuciyarta da har yanzu bai daina bugawa ba hawaye ne taji suna silalo mata, bata san wani mataki zata ajiye kanta ba a wurin Rayyan tsanar ta yayi ko kuma haushin kusancin ta da mahaifiyarshi yake ji bata sani ba, Meyasa zai saka mata boundry da shiga cikin gidan? Me tayi? Da kyar ta kauda tunanin ta tashi ta fara kokarin shirya wardrobe ɗinta tana janye tunanin, a wayanta ta saka karatun qur'ani tana aikin har la'asar kan ta gama ta adana akwatunan ta tafi tayi alwala ta zo tayi sallah, tana zaune taji ana mata knocking ta miƙe taje ta buɗe sai ta ga Abeeha ce murmushi suka sakarwa juna ta shigo ciki. "Cigiyarki na zo yi tun fa jiya rabon da mu haɗu matar bross" Tana ɗan murmushi tace "Da kin taimakeni in kika daina dangantani da wannan Yayan naki, Mammi ma da take faɗa bani da yadda zan yi ne" "Toh Meyasa? Ke ba matar tashi bace?" Abeeha ta faɗa tana zama kan couch na ɗakin. "Gabana faɗuwa yake a duk sadda aka dangantani da shi, ban sani ba tsabar yadda nake jin shakkarshi ne ko yaya" "ke fa ba mu bane Afeefah, ya kamata ki rage wannan tsoron nashi wlh ko mu bama mishi irin tsoron da kike mishi ke matarshi ce sirrin shi, a ina kika taɓa ganin matar dake shakkar mijinta? Lalalalala idan kika tafi a haka ke za ki cutu" "Adda Abee ba za ki gane bane ke kam, ya saleem ɗin ya shigo? Kin ganshi? Ya ci abincin?" Kallonta Abeeha tayi "Eh ya shigo, sun ci har ya tafi ma tun azahar" Ajiyar zuciya ta ɗan sauƙe suka cigaba da hira da Abeehar, Abeehar na nuna mata tayi amfani da trainings da aka yi mata kar kudin Mammi ya tafi a banza ita dai sai dariya take don ko tsireta za'a yi ba za ta iya ba wlh, sai Magrib Abeeha ta tafi ita dai Afeefah bayan tayi isha ta fito ta samu an kawo musu abinci kaɗan ta ɗiba ta koma ɗakin don ko haɗuwa bata so su yi. Daga ranar kullum Saleem sai ya shigo kuma Mammi bata taɓa ƙasa a gwiwar basu tofin ba yayinda bayan an gama abin kari Abeeha ke shiga kitchen da kanta ta musu girki tunda anan yake cin abincin rana har kwana bakwan, kafin ta gama girkin take zuwa ta gaishe da Mammi bayan ta gama ma ta kan leƙa ta kan ta wuce sashenta bata sake zuwa sai gobe tunda ya hana gwara ta bi umurninshi ba tare da ta san dalili ba, a sashenta take zama tayi karatu tayi bacci ta gaji gashi bata iya zaman parlorn don bata so su haɗu kuma kaman ka'ida tun daga ranar basu sake haɗuwa da shi ba har kwana bakwan ya wuce don ko abincin dare ana kai musu zata je ta diba ta shiga ɗakinta ta rufe. Adu'ar ta kuma a koyaushe shine Allah ya dubi Saleem ya yaye mishi wannan bala'in. Ta ɓangaren saleem tun daga ranar da ya fara zuwa wurin Mammi yana shan tofin kuma yana ci a abinci ya fara jin wannan nauyin na zuciyarshi na raguwa, kanshi da kaman an daddaure baya wani tunani mai kyau ya ji kaman ana kwakwance jijiyoyin, bai dai nuna komai ba don tun bayan kwana biyu da ya fara zuwa Sabreena ta saka shi gaba Meyasa yake zuwa gidan aboki yake cin abincin rana bayan bata Gaza ba wurin cinshi? Meyasa ma yake zuwa gidan su Rayyan ɗin abin da baya yi da kaman ka'ida kullum sai ya je? "Sabrina yaushe ya zamana in zan fita ko zan yi mu'amala da wani sai na bi ra'ayinki ne kam? Meyasa za ki damu da abin da bai shafe ki ba? Yau na fara cin abinci a gidan aka ce miki? Toh bana son damuwa da ciwon kai idan maganan da zaki cigaba da yi kenan ki tashi ki bani wuri" Da wani irin tsantsar mamaki take kallonshi Za Ta yi magana ya daka mata tsawa "Ki fita nace!!" Da sauri ta miƙe ta fita har tana haɗawa da sassarfa bata tsaya ko ina ba sai wurin Gaje don babanta baya nan ya fita. "Mun shiga uku! Gaje Ya Saleem yau ni yake yi wa tsawa! Me yake shirin faruwa?" "Ke ki natsu dallah chan me zai faru kuwa? Ya wuci kin je kin dameshi ne yana so ya huta, ki fa sani ko da mallakarshi da muka yi sai kina bin shi a hankali" "Gaje bai fa taɓa ɗaga min murya ba tunda na shigo gidan nan ina tsoron kar wani abu ya faru ne" "Babu abin da ya faru daga ni har mahaifinki muna da yakini kan aikin da aka mana har abada ba zai kwance ba, ki bashi lokaci sai ki koma" Ko da ta bashi lokaci ta koma bai yi mata magana ba, sai ta yarda da cewa ita ce ta takura mishi don haka bata kara magana akan zuwa gidan su Rayyan ba, yau ya shigo gidan sai ya tsaya chak a parlorn yana bin sababbin kujerun da kallo, a hankali ya tsayar da idanunshi kan kujerar da mommy ke yawan zama, tunanin mommyn ya fara sai yaji kanshi ya wani irin sara gabanshi ya shiga faɗuwa zuciyarshi na bugawa da ƙarfi da ƙarfi daidai Sabrina ta fito ganinshi dafe da kujera ya sa tayi hanzarin isa kanshi "Ya Saleem lafiya? me ya sameka? Menene?" "Ƙira min Mommy!" Darammm ta ji zuciyarta ya buga... **** Kawu Labaran ne riƙe da Ghana most go yana kallon Inna Larai dake ta juya kai tana fama da suntumemen ƙafarta da kudaje ke ta sukuwa a kai yace "Ki yi min adu'ar dacewa ai na ji unguwar da ɗaya kawun nashi ya ambata chan zan je in tabbatar da gidan da Afeefar take sai na dawo da ita ta kai ki asibiti don ni dai ba ni da wani kudin asibitin birni! Kin ga dama ke ce uwar ɗakinta..." Inna Asabe ta katse shi "Malam anya za ka yi hankali kuwa? Wani irin zance ne kake yi hakan? Taya Afeefah zata fara taimakon mu bayan duk abubuwan da suka faru? ka manta ita da kake ikirarin itace uwar goyon nata ko ɗakinta bata taɓa bari Afeefar ta taka ba?" "Amma dai mun ciyar da ita kuma mun tufatar da ita, har ɗaki sukutum muka ware mata tayi rayuwa kaman 'ya'yan gidan nan ni ko hassada kike yi min ne ma kin ga zan je birni?" "Allah ya kyauta in maka hassada, ina dai tunatar da kai ne ita Larai ɗin me ya hana 'ya'yan ta yi mata? Mugun alkaba'in da muka bi yarinyar nan dashi shi muke gani a wurin namu yaran daga masu shaye shaye sai masu cikin shege ana ɓararwa a maimakon mu fara tunanin laifin mu mu fara neman hanyar gyara ka sabi jaka don son zuciya zaka tafi neman kudi wurin wacce ka yiwa korar kare a gidan nan..." "Na rantse ko ki min shiru ko in saka sandata in Buge ki, ni zaki faɗawa maganar banza? Idan wulakanta Afeefar ne duk wa ya more ta bayan ku? Ina ce anan kullum take dawo muku da kudaden da take samo muku ni me na taɓa sakata sayar min? Ko ba kece kullum dare kike hayaƙin tafarnuwa da kuka da Ƙashin kifi ba duk saboda Afeefar? Idan akwai waenda ba zata yiwa abu ba sai dai ku, ni kam dolenta idan ma bakin ciki kike min sai na je... Ke kuma Larai ki jirani in dawo" Yana kai nan ya juya ya fice, inna Asabe ta bi shi da kallo kan ta mayar da kallonta kan Inna Larai dake zaune varender ɗinta a yanzu ko tafiya bata iya yi, komai sai an yi mata ga yaran nata kan su yi mata sai ran kowa ya ɓaci sun yi ta mita da kananun maganganu kenan, abinci wannan tunda kawun ba wani ciyar dasu yake ba sai in Asaben ne taji tausayinta ta bata daga wanda ta dafa a 'yar sana'ar da take yi na cikin gida. Wa'azi taji a redio ranan da ya sakata zurfafa tunanin akan sharrin dake bibiyar 'ya'yensu gashi dai sun haifa amma a yanzu babu ɗaya da za'a cire na ƙwarai, sai yanzu wani abu ke shiganta akan neman ilimi barin ma da taji neman ilimin addini farilla ne kan kowani musulmi kuma baka da hujjar kare kanka da rashin sani a wurin ubangiji muddin baka nemi ilimi ba, tunda ta san lokacin da ake sa wa'azuzzukan sai ya zama kullum da hantsi sai ta ji anan ta fara tunanin daga ina ne rayuwarsu ya kuskure tun farko...? Shi dai Kawu Labaran machine ya hau har ya fito kauyen gaba da su ya samu mota da ya kawo shi farkon garin Kaduna ya dire, nan ya tsaya zare ido tunda yake bai taɓa shigowa cikin Kaduna ba bari dai kauyuka yana zuwa sossai musamman na bayansu amma bai taba zuwa babban birni haka ba, zare ido yake tayi yana kalle-kalle wani mota ya tsaya kusa dashi wasu maza huɗu ne ciki "Ya dai ina ka nufa?" "Na zo wurin 'yata ne tana nan cikin gari" "Wani unguwa?" "Ni dai ban tabbatar ba amma kaman unguwar masu kuɗi ne wai G....A...R" Da kyar ya fadi alpabets ɗin suka tuntsure da dariya "GRA kake son cewa?" "Yauwa eh nan fa dai..." "Shigo" Shiga yayi yana washe haƙora yau dai Allah ya nufa gashi a birni basu yi nisa ba ya ga duk sun saka facemask kan yayi magana sun ja window suka fesa mishi wani powder nan ya sulale ya sume... **** Tsaye yake gaban madubi, wanka ya fito daga shi sai towel jikinshi, ginannen jikinshi fari tasss sai daukar ido yake saboda ruwan dake bin murdaddun damatsanshi zuwa parks da ya tara a ciki, madubi ya kurawa idanu yana tunanin irin yanayin da ya shiga a daren jiya wanda rabon da ya ji kwatankwacin hakan sama da shekaru ashirin da biyar, da ƙarfi ya runtse idanunshi da suka yi wani irin jajazir yana fesar da huci daga bakinshi tsaki ya ja a karo na babu adadi ya miƙa hannu zai ɗauki mai kenan aka turo kofan aka shigo da sauri ya ɗago sai idanunshi suka sauƙa kan....! 🖤Gureenjoh🖤 HAIHUWA DA HANJI (A True life story) Fatima Muhammad Gurin (Gureenjoh) Wattpad-Gureenjo6763 Arewabooks-Gureenjoh ADABI WRITERS ASSOCIATION *FREE BOOK* *Alhamdulillah na gode sossai da adu'o'inku gare ni jiki da sauƙi sossai ku lallaɓa da wannan kafin gobe na sake samun ƙarfin jikin, Allah ya bar ƙauna masu kira duk na gode sossai* *36* Ƙoƙarin buɗe idanun da suka yi mishi wani irin nauyi ya fara yana jin yadda fatar jikinshi ya ɗauki raɗaɗi tamkar wanda aka ɗora saman tukubar tsire, kaman ruwa haka tunanin abin da ya faru ya kwararo mishi cikin kwakwalwa har bai san ya buɗe idanun ba tare da yunkura wa ya zauna yana zaro su waje. Wasu garadan matasa ne tsaye kusan su huɗu cikin ɗakin daga kawunansu har kafafunsu a rufe "Su...su su waye ku?" Kalaman suka fito fitt ba tare da ya shirya ba, babu wanda ya amsa sai chan bayan ya gama zare ido yana jin cikinshi na ɗurar ruwa kan ɗaya ya matso ya ja wani kujera ya zauna tare da riƙe haɓar kawu Labaran cikin hannunshi "kai kalle ni nan! Nan ba wurin wasan ka bane idan ka yi abin da muka umurceka lafiya lau zaka fita amma idan ka yi akasin hakan hahahahaa" Ya saki wani dariyar bosawa "za ka yabawa Aya zaƙin ta don ungulu muke bama jewar banza" Wani irin kuuuuuuuuu cikin kawu ya bada ƙara jiki shi ya shiga rawa kar kar kar "Me ku..ke so" A rarrabe yayi maganan harshen shi har yana sarƙewa. "Ba ni lambar yarinyar taka dake GRA!" Ya faɗa yana zaro waya. "Ba ni da shi wlh bani da shi..!" Kawu ya basu amsa har lokacin jikinshi bai daina rawa ba. Kallon kar ka raina min hankali yayi mishi kafin yayi wani yunkuri mutumin ya sauke mishi wasu zafafan maruka da ya sa ya daina ji da gani na mintuna, wani ƙaraa yake ji suuuuu a cikin kunnenshi da kyar ya iya jiyo zancen mutumin cikin hargagi "Ni za ka rainawa wayau?? Ka manta abin da na gama ce maka ko? Toh kan in sauya kamanninka maza maza ba ni layinta" Kuka kawu ya fashe dashi da karfi bayan dawowa hayyacinshi yana rantse rantse babu irin azabar da ba su mishi ba amma shi ya san bashi da wani Layin Afeefah, da kyar suka kyale shi "Ka yi maza ka fara tunanin Layin nan in ba haka ba sai na tabbatar na sauya maka kamanni yadda babu mai iya gane ka! Kuma zan saka flyer in tsige faratunka ɗaya bayan ɗaya kan in jefawa kungiyar mu kai su san yadda za su yi da jini da tsokar ka don na faɗa maka idan ma kana kokarin ɓoye kudinka ne za ka ba da jiki da jininka...." Kawu bai san yana fitsari ba don tsabar tashin hankali, bilhakki yake kuka yana neman afuwa sai da suka gama azabtar dashi suka juya suka fice suka bar shi nan yashe. Bai san adadin lokutan da ya dauka cikin azaba ba, chan ya ji ana kwarara mishi ruwan sanyi a razane ya farka "Wlh zan...zan ba da Layin... Zan ba da layi" Numbern su Larai ya bayar aka ƙira aka saka shi yin shiru. "Yanzu haka mijinki na hannun mu muna bukatar kuɗi kimanin Naira Miliyon goma ko kuma ku da ganinshi har gaban Abada..." Salati ta kwarma da ya ja hankalin Inna Asabe da sauran yaran suka taho. "Ke! Natsu!!" Ya sake daka mata tsawa tuni ta shiga taitayinta ya miƙawa kawun waya a rikice cikin tashin hankali yake cewa "Larai ku taimakeni... Akwai kudi a ɗakina ƙasan gado ina da 'yar rami a ciki akwai tulu na binne za ku samu kuɗi...ku..ku haɗa har da gonan gado na ku sayar da gidan da muke ciki ku basu duk abinda suka roka don Allah...zasu kashe ni ku taimakeni" da kuka sossai ya ƙarasa. Inna Larai manta halin da suke ciki tayi "Au dama kana da wannan uban kuɗin ka ƙi kaini asibiti? Lallai ka cika azzalumi..." "Ke kina da hankali kuwa?" Ya ƙare maganan yana sanyawa kawu bindiga a makoshi wani irin ihu ya kwarma yana cewa su taimake shi kar su kashe shi "kun ji abin da yace ai ko? Toh idan kuna son shi ku aikata ku kawo mana kuɗin idan kuma akasin haka za ku tsinci wasu sassa na jikinshi a cikin Ghana most go...kuka sake kuka sanar da 'yan sanda dukkanku sunayen ku gawarwaki..." Yana kai nan ya katse wayan suka fice suka bar kawu cikin halin ha'ula'i sai kuka yake wane karamin yaro don bai taɓa zaton haka tashin hankalin kidnapping yake ba. A chan kuwa Dutsen-wai tunani suka fara na yadda za su nemi masu sayan gona da gidan da suke ciki, inna Asabe ta tafi ta ɗauko kudaɗen da yake magana duka duka basu fi dubu dari biyar ba a hakan ma mamaki suke na yadda ya iya boye irin kudin suna cikin talauci da wahala, nan yaran suka tashi akan ba za'a sayar da komai ba idan kwananshi ne ya ƙare Allah ya ji kanshi amma ba zai mutu ya bar su basu da komai ba idan ya mutu su yi yaya? Zazzafar kace- nace ne ya barƙe har suka manta ma Ubansu na chan hannun 'yan sari. Kwanan kawu ɗaya a wurin ruwa kawai suke bashi duk ya firgice ya jeme ga yana dakuwa don lillahi in suka tashi jibgar shi kaman buhun hatsi suka samu, a rana na biyun ne suka sake dawowa sai dai duk kiran da zasu yiwa su inna Larai sun ƙi picking. "Banza marar Amfani iyalan naka ma ba kaunar ka suke ba..." Ya faɗa yana ball dashi ihu ya kwarma yana basu haƙuri inaa suka saɓe shi suna zura mishi wani bakin kyalle a kai sai wani ɗakin na daban, ko da suka buɗe mutane uku ya gani a tare da shi zaune duk a jeme kawunansu kwal-kwal, shima aski aka yi mishi tal aka bashi wani riga mai kaman dogon riga ya saka a kausashe waenda suke gadin wurin alamu sun fi waenchan zafi suka ce "Jininka ya halalta a yau zaka bakunci lahira..." Bai san wanchan tashin hankalin da ya shiga mai sauki bane a yanzu ba zai iya fasalta halin da yake ciki ba barin ma da mutanen da ya samu suka ce mishi tunda har sun furta zai mutu yau sai ya mutu basa magana biyu, yankashi zasu yi su ba dodo jinin shi naman kuma suyi romo su cinye don matsafa ne wani irin zawo ya barƙe dashi tsabar kaɗuwa ya gigice sai haƙuri yake basu kuka kam har ya rasa hawaye amma sun ƙi kula shi a gigice yake cewa "Yanzu na san asalin tsafi...ashe Afeefah babu abin da kike yi? Na shiga uku wayyo Allah! Afeefah baki isa yin irin wannan ba...wannan ya fi karfin tunaninki...Na shiga uku na lalace wayyo Allah na..." Kuka bilhakki yake yana kiran sunan Afeefah a gigice don dai gashi nan da layun kariya daga mayun ya fito daga gida incase mijin ma maye ne kar su cinye shi sai gashi yana kallon asalin maita, suna shirin cinye shi banzar layunshi sun kasa mishi anfani, bai san adadin kuka da magiya da yayi tayi ba babu sunan wanda bai kira ba har aka zo aka sake fita dashi zuwa ɗakin tsafin nan ya ƙara firgita ganin wasu irin halittun dodanni ga wasu masu jajayen kaya da baƙake marasa imani jibga-jibga sai muzurai suke suna ganinshi kaman sun ga nama ko kuma ya ce naman ma suka gani, yana tirjewa yana tsandara karar a taimakeshi amma chadak suka ɗaga shi kaman kayan wanki har gaban shugabansu. A tsaye yake amma suna haɗa idanu bai san ya zube ba. "Ka taimakeni ka ji kaina wlh ni maraya ne, ba ni da kowa iyalina ma basu da kowa bayan ni kar ku kashe ni, kar ku sha jinina na tuba...!" Har a ranshi magiya yake yana kuka da majina dariya suka sheke dashi wata murya dake fita bibbiyu ya daka mishi tsawa... "Yi mana shiru!! Ka riga ka shigo nan babu fita ka sa a ranka za ka bakunci lahira a yau jininka kuwa zai zama abin sha mafi gardi ga shugabanmu a wannan dare yayin da za mu kashe dare cikin party da namarka..." Suuuuu haka kawu ya sume sai dai duk yadda zai sume baya seconds zai farka da karfin tsafi... A haka aka ɗauke shi zuwa gaban wani tukunya dake bararraka da baƙin abu aka zaro wata shirgegiyar wuƙa dake sheƙi aka ɗora mishi a wuya, ya gigice! Ya ruɗe! Ya fice daga cikin hayyacinshi! Zuciyarshi kiris ta rage ta fita daga madaukarta, kashi da fitsari kam bai san adadin da yayi ba barin ma da ya ga da gaske mutuwar zai yi... **** "Mommy...! Mommy...!!!" Da ƙarfi yake kwala kiran sunan yana zagaye gidan don jinshi yake kaman zai yi hauka idan bai sanya mahaifiyar tashi a idanu ba sai dai yana buɗe ɗakin mommy gaje ya gani zaune tana ma cin nama ne soyayye a plate. "Ina mommy?" Shiru tayi daidai Yaya ya fito shima daga ɗakin da ya san dai na Sadiqa ne. "Ina 'yan uwana? Ina mahaifiyata?" Ya yi maganan da ƙarfin gaske da ya sa suka zabura suna dawowa hayyacinsu ganin yadda ya zama lokaci guda Yaya ya dafa shi "ka natsu mana Saleem, mu ma ai iyayenka ne tunda iyayen matarka ne ka manta kai ka fitar da su mahaifiyar taka daga gidan nan ka ce mu dawo mu zauna tare?" Wani irin riƙe kanshi yayi dake flashing mishi duk abubuwan da suka faru tun daga auren Sabrina, ji yake kaman zai yi hauka da kyar ya fara ambaton "Innalillahi wainna ilaihi rajiun! Hasbunallahu wani'imal wakeel...!" Kai tsaye gaban Sabrina da jikinta ke rawa ya ƙarasa yayi mata wani irin mugun riƙo da tana tunanin kila hannunta ya karye a tsawace yace "Me kika min? Me kika aikata min!!" Yadda yake zazzaro idanunshi da suka zama Red ya sa ta sake firgita. "Saleem me za ta yi maka k...." "Shuttt up!! Ku yi min shiru a yau na rantse da Allah sai kun faɗa min me kuka yi min? Me kuka yi min da ya sa na zaɓe ku kan uwata da 'yan uwana??" Sabrina zata yi magana yayi wurgi da ita har ta bugi kujera tana zubewa ƙasa, kofan parlorn yaje ya rufe da key ya koma da hanzari ya rufe na baya ya zo ya haura ɗakinshi kaman zararre ya samo belt ya sauƙo da gudu ya rufeta da duka yana ihun tambayar me ta mishi me suka mishi? Don ko jikinshi kunnuwa ne ba zai yarda da gangan yayi duk abin da yayi ba ta gigice duk inda zata gudu ta ɓuya ta gudu amma sai ya fusgota yana dukan yana tuna irin dukan da yayiwa Sadiqa, babanta da mamanta suka makure wuri guda suna kallon yadda yake jibgar 'yar su idan tayi wurinsu da gudu suma sai su runtuma kar bulala ya same su da ta ga no go ta fara ihun "ba ni ce nayi ba wallahi su ne... Su gaje ne su suka yi komai su suke karɓo magani wurin bokaye muka mallake ka wlh su ne...." Dakatawa yayi yana kallonsu "Me take cewa?" Duk ya haukace tsoro ya rufe su, bindiga ya zaro "Ko ku faɗa min me nayi muku da kuka zalunceni ko kuma dukkanku in kashe ku... Me na muku???" Da wani irin tsawa yayi maganan duk suna zube a ƙasa a gigice don yadda yaken nan tsaff sai ya harbe su, a darare Yaya ya fara cewa "Kayi haƙuri Don Allah ka yi haƙuri.." Gini ya harba karar bindigar ya saka Yaya fitsari Sabrina da Gaje suka tafi a sume, ruwa ya kwaso ya zo ya kwarara musu yana nuna gini "Kun ga yadda ginin nan ya fashe ko? Toh billahi ko ku faɗa min ko in fashe kawunanku haka" "ka saurareni ka yi hakuri zan faɗa wlh zan fada maka..! Mahaifiyarka da ni mun kasance 'yan uba tun da muka tashi iyayenmu mata ke nuna mana ba ɗaya muke ba, hakan yasa muka tashi da wani irin ƙin juna a zuciya, sai kuma Allah ya daukaka Hussaina hakan ya ƙara mini hassada da kyashinta barin ma da muka rasa iyaye bata daukeni dan uwa kuma abokin shawarar ta ba, bata kula ni ko 'ya'yana sai in bukatarta ne ya kawo ta wurin mu, ta daukeni tamkar ɗan gidanta bata girmamani babu ruwanta da kyautata mini tana nuna min itama wahalar ta ya sama mata in tashi in nema anan na ƙudiri aniyar mayar da dukiyar ta nawa, mun yi shige shige dayawa a baya kasancewar kana yawan zuwa duk ruwan da za mu baka akwai wani asiri ciki sai dai duk basa kama ka saboda kana neman kariya kuma kana Adu'a, har ma mun fitar da ran samunka muke tura yarinyar mu nema mana kuɗi da surarta don muna so itama ta auri mai kuɗi mu kerewa Hussaina(Mommy) sai kwatsam ta dawo da son zuciyarta garemu... Mun yi amfani da hakan Allah kuma ya bamu dama saboda ba don Allah ta neme mu ba muka juye ka ka zama sai abin da Sabrina ta ce..." Hawaye ne ke sauka mishi a haukace yace "Ni na zama kwallonku kenan?? Ni ne da nake tausaya muku nake taimakonku daidai gwargwado kuka zaɓi salwantarwa da tura ni cikin fushin ubangiji??" "Kayi hakuri don Allah! Ka yi hakuri..." "Ku tashi ku fita a gidan nan har abada kar ku bari fuskata ta kalli naku... Duk ranar da hakan ta kasance sai na sa bindigata na harbe ku ku fita nace!!!" A gigice suka miƙe suna ji suna gani suka fita da kayan jikinsu kawai don ko cokali ya hana su ɗauka duk tatsarshi da suka dinga yi na kuɗi suna boyewa duk yana cikin gidan, ko takalmi babu kafafunsu haka suka fita rike da Sabrina da ta sauya kamanni tana ta kuka barin ma da ya furta ya sake ta saki biyu ta je ta ƙarata.. (Ƙarshen alewa ƙasa!) Su mommy suna zaune suna kallon sunna Tv da ake hasko wa'azin likitan zuciya wato sheikh tijjani Ahmad yusuf guruntum kawai suka ga an turo kofa an shigo, a razane suka miƙe tsaye sai ganin Saleem suka yi yana tahowa yana haɗa hanya a rikice mommy ta nufe shi "Saleem..! Saleem...!! Kai ne? Kai ne da gaske.." Taro shi tayi ganin zai faɗi yana furta "Mo..myy" Sai ya sume musu.. 🖤Gureenjoh🖤 HAIHUWA DA HANJI (A True life story) Fatima Muhammad Gurin (Gureenjoh) Wattpad-Gureenjo6763 Arewabooks-Gureenjoh ADABI WRITERS ASSOCIATION *FREE BOOK* *37* Bayan ta tashi daga baccin da ya dauƙeta tun bayan Sallar asuba wanka tayi ta shirya cikin wata doguwar riga mai hannun roba purple da ya amsheta ta ɗaura dankwalin a kanta sai ta nufi sashen mammi don gaisheta, da sallama ta sanya kanta ciki ta ga mammin kwance a kan sallayar da tayi sallah ta ɗora kanta saman pillow tasbihi take a hankali tana ta maimaita "Allahumma inni As'aluka husnal khatima, Allahummar ruzuƙnee taubatan nasuha qablal maut, Allahumma ya musalibbal quluub thabbit qalby ala dinika, ya musarrafar quluub sarraf quluubina ala ɗa'atik..!" Abin da ta lura kusan kullum a kwanakin ya zama tasbihin Mammi kenan, a ganganta ta zauna "Mammi...kina lafiya?" Tayi tambayar hankalinta na kan mammin gabaɗaya ganin yanayinta kaman marar lafiya lumshe idanu mammin tayi ta buɗe kan ta ce a hankali "Afeefah je ki buɗe bedside za ki ga wani kwali ki ɗauko" Miƙewa tayi taje ta buɗe ta ɗauko ta dawo tana zama riƙe dashi "Mammi gashinan!" Mammin bata motsa daga kwancen ba don bata jin zata iya tashi tace a hankali "Afeefah ki buɗe ki gani menene ciki?" Buɗewa tayi sai ta ga set ne na dankunne sarka da abin hannu da kuma zobe, daga gani ka san ba ƙarami bane don ma bata san gold ba da sai ta ce wannan ɗin gold ne babba ma don yadda yayi wani irin kyau ga ɗaukar ido. "Set na sarka ne Mammi" "Masha Allah, sadakinki kenan da na yi amfani dashi na saya miki wannan kadarar, ki riƙe a wurin ki naki ne halak malak ban baki tsabar kudin bane don na san ba zai ajiyu ba amma wannan ko shekara nawa zai yi a zaune babu abin da zai yi sai ma darajar shi ya ninku" Rasa bakin godiya Afeefah tayi sai hawaye ya shiga ziraro mata "Mammi kin yi min komai a wannan duniyar ba ni da abin da zan saka miki face Adu'ar Allah ubangiji ya baki lafiya, Allah ya yaye miki wannan ciwo ya kawo mana karshensa mu ga kema kin warke kaman kowa, Allah ya sa kaffara kika yi" "Ai lafiyar ta zo ma Afeefah" Ta faɗa tana rufe idanu jin yadda take jin ciwo mai tsanani a ciki da ma jikinta gabaɗaya. "Mammi...!" Sai ta ga wani irin zufa na karyo mata numfashinta na fita da kyar da kyar har chasbin hannunta na zamewa da kanshi, wani irin tashin hankali ne ya ziyarce ta da gudu ta miƙe ta fito sai tayi side ɗinsu kaman za ta kifa haka ta tura kofan ta same shi tsaye gaban madubi, ba zata ce ga yadda ta riske shi ba ita dai ta san ta isa gabanshi tare da riƙe hannunshi "Mammi...! Mammi.." "Me ya sameta?" Ya faɗa hankalinshi na tashi lokaci ɗaya, ganin duk ta ruɗe yace "Je ina zuwa" Fita tayi da sauri shi kuwa ya ɗauki boxers kawai ya saka da jallabiya tare da zaran keyn mota kafafunshi ma silifas ce ta wanka ya fice da hanzari, yanayin da ya sameta sai da ya ƙara ɗaga masa hankali haka ya ɗauketa Afeefah na ta kuka suka nufi Asibiti duk ma'aikatan hankalinsu ya tashi da sauri aka karɓeta sai oxygen aka sanya mata sun yi iya kokarinsu har numfashinta ya ɗan daidaitu, Rayyan dai ya kasa aikata komai don ba karamin girgiza yayi ba duk tashin ciwonta bai taɓa ganin kaman wannan ba, bai zaci za su iso asibitin da ranta ba jikinshi rawa kawai yake yana tsaye daga gefe yana kallonsu a sadda zuciyarshi ke cigaba da bugawa kaman zai fashe, idanunshi sun rine sai adu'a yake yana roƙon Allah akan ya bata sauƙi a ranshi. Ganin ta dawo daidai oxygen ɗin na tafiya a hankali ba kaman daga farko ba da in ta ja kaman ba zata sauƙe ba ya isa gangarta ya riƙe hannunta kawai ya zauna, a jikin gadon ya ɗaura kanshi yana danne abinda yake ji na taso mishi, ina ma da zai iya kuka da yayi ko don samun sassaucin abinda yake ji a ranshi da ma kwakwalwanshi! Ba zai ce ga adadin lokutan da ya ɗauka zaune a wurin cikin wannan yanayi ba chan dai ya ji kaman ana shafa suman kanshi da ɗan hanzari ya ɗago sai suka haɗa idanu tana ta kallonshi, gyara zama yayi yana kirkiro murmushi mai nauyi ya ce "Mammi na! Kin farka? Ya jikin?" Ta sake yin murmushi a hankali ta nuna mishi oxygen na hancinta sai ya cire yana jin yadda take sauke numfashi a kai akai "Mammi ki yi saving energy ɗinki kar ki yi magana kin ji?" Ta sake yin murmushi "Ina so na ji abin da ke bakin ka! Ka ba ni labari...tun jiya na lura kana son min magana amma kana riƙe wa menene?" Shiru ya ɗan yi "Speak up Saraki, yanzu ne kake da lokacin magana da ni anjima kaɗan kila sai dai matarka ko 'yan uwanka" Da sauri ya ɗan kalleta tana ta murmushi, kanshi ya duƙar a hankali ya fara furta "Mammi ki daina irin wannan maganan don Allah" "Toh na daina Saraki!" Ta faɗa tana lumshe ido, hannunshi dake cikin nata ne ya ƙara yin sanyi she can feel the nervousness a cikin tafin hannunshi zata iya cewa yana cikin yanayi ne marar fasaltuwa sai dai da yake namiji ne kuma jarumi yana iya shanye damuwarshi kaman babu komai. Idan Mammi ta tafi ba tare da ya sanar da ita menene a ƙasan Ranshi ba tabbas zai yi nadama mai girma, tunaninsa ya dinga rarrabuwa har yana jin kaman zai zauce idan ya cigaba da zurfafa a cikin muguwar tafiyar rayuwarshi...iya tunanin kaɗai kan karya duk wani guntun karsashinsa. ***** A hankali yake buɗe idanunshi har ya ware su akan Mommy da su Sadiqa dake zaune a ɗakin jugum jugum. "Saleem! Ka farka? Sannu ko mu je asibiti ne?" Girgiza kai yayi yana Miƙewa zaune jikin gadon ya kalli mommy da ita ma take kallonshi a hankali yace "Mommy na tuba! Mommy ki yafe min wallahi...." "Shhhh Saleem na sani, na san ba da saninka ka aikata hakan ba na san baka cikin hankalinka a lokacin da komai ke faruwa, laifina ne wlh laifina ne ka yafe min Saleem son zuciya ɓacinta, hakika na yi amfani da son zuciyata wurin ɗaiɗaita maka rayuwa don Allah ka gafarceni" Ta roka yafiyarshi tana kuka su ma duk su sadika suka shiga bashi hakuri, anan ya zauna yana jin yadda komai ya kasance... Hakika mommy ta yi kuskure Afeefah ce ta faɗo mishi a rai ko tana cikin wani hali yanzu? Ko ya rayuwa yayi da ita? Allah masani ****** "Mammi..!" Ya sake ƙira a karo na biyu ba tare da ta buɗe ido ba tace "Uhmm" "Zan faɗa miki ne, zan faɗa miki wanene ni..." Da sauri ta buɗe ido ta kalleshi cikin yanayin jin jiki ta zura mishi idanun a hankali ya cigaba da cewa "Ban manta komai ba, na ƙi faɗa ne saboda wacce daraja da ƙimarta suka zama ƙololuwa a gare ni ta yi fatali da hakan ta ɗauke ni ta yasar tamkar tsumma a cikin al'ummar da ba ni da masaniyar yaya suke bare ya rayuwarsu take, ya al'adarsu take ko ya imaninsu yake, ba tare da ta damu da zan ci ko bazan ci ba, shin rayuwata za ta inganta ko za ta yi lalacewa marar iyaka? kafin na haɗu da ke na zaci uwa masifa ce ga 'ya'yanta ta kan nesanta su da farin ciki ta saya musu wahala, ta kan zama tamkar ginin ƙasa da muddin ɗa ya jingina da ita sai ya faɗi, a maimakon ta kasance garkuwata sai ta zama ita ce a farkon cutar da rayuwata, na kasance a koyaushe bana rufe idanu na buɗe ba tare da na ga sadda take cire hannayenta daga cikin nawa ba tare da tura ni cikin dattin juji...ta tafi! Ta tafi da rayuwata da dukkan farin cikin da ya taɓa wanzuwa cikinsa ta tafi da rai da ruhi na..." Shiru yayi yana cije lip ɗin shi na ƙasa da har su ma rawa suke yi. "Ke ce kika ba ni hope na rayuwa, a kan ki na yarda uwayen ma suna suka tara Mammi kin zame min gata a sadda na kasance cikin wahala, kin ba ni duk wani kulawa da gata ba tare da tsammanin lada ba kin bani kaunar da bata taɓa yankewa ba, kin zame min rayuwa, rahama da kyautatawa da bata da iyaka. Mammi Sunana Sameer..." Lumshe ido tayi a hankali hawaye na sauka mata ya sa hannu ya share mata. A hankali ya cigaba da bata labarin da kafin ya gama jijiyoyin kanshi sun yi raɗa-raɗa, idanunshi tamkar garwashi muryarshi har yankewa yake amma Dukda haka jarumtarshi ta ƙi barin ruwan hawaye ko guda ya diga bisa fuskar shi ko zai samu salama cikin rai da ruhinshi, ba zata iya Miƙewa ba da zata iya da ta rungumeshi ta rarrasheshi da ta nuna mishi komai na duniya mai wucewa ne, da ta tuna mishi da irin girma da darajar da Allah ya ba uwa don kalamanshi sun yi tsauri sossai a kanta, bata san dalilin ta na yin hakan ba amma ta san babu uwar da zata so tagayyarar ɗan ta, ɗan ma mai tarin gata, daraja da martaba irin Rayyan. "Ka zama mai haƙuri da rayuwa! Ka zama mai afuwa Saraki haƙiƙa an cuce ka an kuma ɗauki alhakinka mai yawan gaske amma ina roƙon ka da ka bari komai ya wuce kaman ba'a yi ba, ka yi uzuri ga mahaifiyarka ka waiwayi gida..." Shiru tayi sai ta ɗan yunkura kaman zata tashi ta koma ta kwanta tana shaƙuwa. "Ka min alƙawari Rayyan!" Girgiza kai yayi yana ɗago rinannun idanunshi gareta sai ya ji tana ambaton Allah da salati ɗauke a Bakinta a kan idanunshi, hannunta na a cikin nashi Mammi ta ja numfashinta na ƙarshe da ya tafi da duk wani ƙwarin gwiwanshi, ya tafi da duk wani haske da yake tunanin da shi yake amfani wurin haskaka tarin duhun dake mamaye da shi, gigice wa ya nemi yi sai ya manta da cewa shi ɗin ma likita ne, ya kasa yanke hukuncin cewa ta tafi ya kasa yardar wa kanshi cewa da gaske ta tafi ta bar shi... "Innalillahi wainna ilaihi rajiun..." Shine kalaman da ya fito da kyar ya ratsa harshenshi har ya fita sarari. Ya fi mintuna ashirin a zaune a haka baya iya ko da kifta idanun kirki, kila mafarki yake, kila bacci tayi za ta buɗe idanu kila zai iya ganin kirjinta ya motsa ya cigaba da bugawa kila za ta ja numfashi ta ce mishi wasa take... Shigowar wani likitan ne ya tabbatar mishi da cewa da gaske ya rasa Mammi rasawa ta har abada haƙiƙa ɗaci da raɗaɗin mutuwa ba za su faɗu ba ba kuma za su misaltu ba. A chan reception kuwa Su jannah da Afeefah ne zaune cikin damuwa mai yawa don tunda suka shigo Afeefah bata daina zubar da kwallah ba, ta san mutuwa kuma ta ga mutuwa daban daban bata fata ya kasance a kan Mammi nan kusa Dukda ta san da cewa mutuwar dole ce ga dukkan mai rai, su uncle Musa da iyalan shi da Abeeha ta ƙira ta sanar musu jikin Mammi babu daaɗi duk suna cikin asibitin a lokacin da wannan likita ya fito ya sanar musu da rasuwar gigice wa suka yi suka fice daga hayyacinsu, Jannah ce ta yanke jiki ta faɗi sai jini ya fara fita mata Abeeha kam rasa ma ya zata yi tayi sai da uncle Sanusi ya riƙo ta yana ta maimaita salati ta kankanmeshi ta fara kuka mai tsuma zuciya shikenan sun zama marayu babu uwa babu uba, Mammi ta tafi lallai dukkan mai rai mamaci ne. Afeefah kam ba zata ce ga yanayin da take ciki ba, Dukda ta kaɗu iya kaɗuwa sai dai ko motsi ta kasa yi daga inda take hawayen idanunta ma kafewa suka yi, wata cousin ɗin su Abeehar ce ta riƙe mata hannu sai ta firgita tana kallonta idanunta duk a waje... "Wai cewa suke Mammi ta rasu? Ko kunnuwana ne basu ji da kyau ba?" "Sai haƙuri Afeefah, sai haƙuri..." Wasu irin hawaye ne suka shiga zubo mata masu zafi da raɗaɗi, da kyar take iya maimaita innalillahi wainna ilaihi rajiun.... A lokacin Rayyan ya fito hannunshi na tura gadon da mammin take kai a hankali yana tafiya ne ba tare da ya san inda yake jefa kafafunshi ba, Uncle Sanusi ne da matarshi suka taho da sauri suka saka mishi hannu don kaman zai kifa, idanunshi sun zama wani iri jikinshi na rawa zuciyarshi a bushe haka suka fice yana gaban motar da Mammi ke ciki wacce amblance ce aka dauko ta a baya har cikin gida, a ɗakinta aka sanyata babu wani jinkiri Matar uncle Musa dattijuwar malama da taimakon wasu malamai mata aka yi mata wanka aka yi mata sutura, kan kace mene gidan ya dinke da mutane masu kuka na yi masu yabon kyaun halinta na yi, Jannah dai tana asibiti don ɓari tayi ba tare da ta sani ba. Abeeha da Afeefah banda kuka da du'a babu abinda suke yayinda Rayyan na a parlorn shi a zaune wane mutum-mutumi tasbihi yake yi amma ba zai iya cewa ga abin da yake cewa a ciki ba, Saleem ne ya shigo Dukda ba ƙarfin jiki ya samu ba sai dai labarin mutuwar ya dugunzuma hankalinshi. "Rayyan!" Ya kira sunan. Jajayen idanunshi ya buɗe ya zura mishi ba tare da yayi magana ba "Sannu! Allah ya gafartawa Mammi Allah ya haskaka makwancinta ya sadata da annabin rahama" Da kyar ya iya furta "Ameen" Idanunshi na kan hawayen da Saleem ɗin ke yi ina ma zai iya? Ina ma ya san ta yadda zai nemo hawayen? Ina ma zai iya cire zuciyarshi ya yasar? Da yayi hakan ko zai huta raɗaɗin da ke gasata wane wuta. "An gama shirya ta ayi alwala a fita gabatar da sallah don samu a kaita makwancinta!" Wannan kalma ta Uncle Mansur ya zama kaman zuban wuta a jikinshi, shikenan fa yanzu ko? Shikenan zai rabu da Mammi rabuwa ta har abada? Saleem ne ya ja hannunshi har zuwa bayi yayi alwala suka fito a tare zuwa ɗakin Mammi aka ɗago makarar aka nufi fita da ita haraba inda kuka ke tashi, kowa idanunshi na kan Rayyan ne da yake ta focusing akan hanyar da yake takawa kar ya faɗi riƙe da gawar Mammi da yayi mata sallama na ƙarshe da qulhuwallahu ahad! A tare da shi aka yi mata Sallah aka kaita makwancinta na gaskiya, shine ya ba da ghdumuwa wurin sakata a rami kuma shi ne ya fara zuba mata ƙasa kan yayi baya baya zai faɗi aka tare shi su Uncle Mansur ne da Saleem, ɗagowa yayi yana kallonsu kila su basa jin abinda yake ji tunda gashi suna hawaye! Har aka gama binne Mammi aka kamo Rayyan zuwa mota baya gane fari ko baƙi don duk wanda zai ji mutuwar Mammi a bayan Rayyan ne.... Innalillahi wainna ilaihi rajiun 😭 Allah ka sa mu yi kyakyawar karshe! 🖤Gureenjoh🖤 HAIHUWA DA HANJI (A True life story) Fatima Muhammad Gurin (Gureenjoh) Wattpad-Gureenjo6763 Arewabooks-Gureenjoh ADABI WRITERS ASSOCIATION *FREE BOOK* *38* "Dakata!!" Wata murya mai amo tayi maganan. Chakk suka tsaya daga ɗora wukan a maƙogoron kawun. "Mecece alaƙarshi da ƙungiya?" Yayi tambayar a kausashe. "Babu mai girma shugaba" "Ku kyaleshi jinin shi bai halalta mana ba" Suman daaɗi ne ya tafi da kawu Dukda azabar da yake ciki, dunkule shi suka yi suka tura cikin buhu aka saɓe shi kaman kayan wanki aka fitar sai haushi suke ji bai musu amfani ba tsabar lalacewarshi, a booth na mota aka saka shi sai da suka yi tafiya mai uban nisa kan suka buɗe booth ɗin suka cilla shi ƙasa suka yi tafiyarsu. Ya fi awa nawa yana mutsu-mutsu ga zafin rana Allah ya kawo wani mai ruwa ya taimake shi ya buɗe buhun sai ya fara tari da mayar da numfashi sama sama, da kyar yake ambatar "Ruwa! Ruwa!!" Mai ruwan ya bashi ruwa a gora ya sha sossai yana sauke numfashi kan ya fara kalle kallen wurin da yake, wani kauye ne na daban "Me ya saka ka cikin buhu bawan Allah?" "Sace ni aka yi 'yan yankan kai ne suka sace ni Allah ya kubutar da ni" Abin mamaki ya ɗauke shi har gidan mai garin garin suna da karamci aka bashi wuri yayi wanka ya wanke najasar jikinshi ya rama sallaolin da suka hau kanshi, har abinci ya ci aka ba shi kuɗin mota ya nufi Dutsen-wai cikin zuciyarshi saƙe-saƙe ne mai yawan gaske ga bakin cikin abin da su larai suka yi mishi ga yadda ya sha jinin jikinshi da abin da ya riska a kwanakin wanda har abada ba zai taɓa mantawa ba, yana isa Dutsen-wai gidan mai gari ya nufa yana neman iso aka mishi iso ya ce "Toh dama na zo ne in sanar kuma in nemi a gargaɗi duk jama'ar garin nan cewa duk wanda ya sake cewa Ɗiyata Afeefah Mayya sai mun yi shari'a har kotun koli don Afeefah ba Mayya ba ce, ita kuma ba Annoba ba ce" "Toh fa da kanka Malam Labaran? Kana lafiya kuwa?" "Lafiyata ƙalau kawai dai na san Afeefah ba Mayya ba ce kuma kar a sake ce mata haka don abin da Mayu suke yi ko a mafarki ba zata iya ba wannan abu ne da ya shallake dukkan tunanin mai tunani." Ya ƙarasa cikin tabbatarwa da jimami. "Dama tun farko tsantsar jahilci da son zuciya ya sa kuka lakaba mata abinda ba shine ba, ashe kenan mutum ba zai taɓa mutuwa haka siddan ba? Har fa tambari kuka buga na cewar tun tana ciki ta cinye ɗan uwanka amma Alhamdulillah tunda ka gane gaskiya kuma kana shirin tsayawa a kanta sai ka yi wa kanka faɗa ka nemi tsari da jahilci don wallahi mugun ciwo ne kuma shi ke ɗawainiya da mafi yawanku cikin wannan ƙauye". Malam liman ne ya jero wannan jawabin, kawu ya gamsu har ya ji jikinshi na ɗan sanyi barin ma da malam liman ya sake nusar dashi akan Allah shi ba ruwanshi, da ya turo mu duniya yayi mana umarnin mu nemi sani a kanshi kafin mu bauta mishi, ba ka da hujjar kare kanka da rashin sani a wurin Ubangiji matukar baka tashi ka nema ba. kan ya dawo gida labarin dawowarshi ya riske su bai damu da zancen mutane ba da wasu ke cewa kila ta cika shi da kuɗi ne wasu na zaton ko don ta auri mai kuɗi yanzu ai dole ya ja ta jiki. Shi kuwa hankalinshi ya fi tafiya ga jan hankalin da liman yayi mishi na neman ilimi Dukda a yanzu wani tataburzun ne gabanshi don saurin da yake zabgawa yana so ya tabbatar babu kowa ne a gidanshi kafin faɗuwar rana. Kaman daga sama suka ganshi ya faɗo Asabe murfin tukunya ce a hannunta sai da ya subuce ya faɗi ƙasa ya tsaya kyamm yana kallonsu "Toh ban mutu ba! Kuma dama an ce sai abu ya same ka kake sanin masu sonka ashe dukkanku maƙiyana ne na tara? Ashe za ku iya bari na in mutu? Toh an gama wallahi gwara in zauna ni kaɗai na da in cigaba da zama da ku don haka kowaccenku ta tattara ya nata ya nata ta bar min gida na sake ku saki ɗaiɗai..." "Innalillahi wainna ilaihi rajiun Malam ka tsaya ka saura..." Ya katse ta da masifa "Babu abin da zan saurara Asabe! dole ku bar min gida a yau ba sai anjima ba kuma ku tattaro yaranku kaf ku fice min daga gida a tabbatar kuma an dawo min da kudade na mugayen banza mugayen wofi" Sai masifa yake ko ya tsaya ya saurare su abin ya mishi zafi rigima fa sossai ya kachame don suma sun ce in zasu tafi ba zasu tafi da yara ba tunda ba da su suka zo a kullin gararsu ba ko hutawa bai yi ba aka sake komawa gaban manya ya rantse shi ya sake su su tafi kuma baya bukatar ko wani ɗa don za su iya saka wuyanshi gabas su yanka tunda suka iya watsar da rayuwarshi alhali yana chan cikin tsaka mai wuya. "Labaran!" Malam liman ya kira shi ya amsa "ka san ko ma menene suka yi laifinka ne?" "Ta yaya? Ina fa chan gaban azzalumai mutanen nan don basu da imani suka ƙi daukar waya alhali ga abin da nace su yi da kuɗina ba nasu ba su kubutar da ni, ba don Allah na so na da sauran numfashi ba da na jima da mutuwa yanzu zaman makoki ake" "Labaran ka yarda kaso mai girma na abin da ya faru laifinka ne" "shiyasa na ce ina so in ji ta yaya?" ***** A ɓangaren Rayyan ba zai ce ga yadda yinin ya kasance mishi ba don baya gane komai, kawai yana so ya ji an daina ko magana a gangarshi ya ji shiru na ratsawa don ya samu damar gamsar da kanshi cewa da gaske ya rasa mace ɗaya jal mafi muhimmanci a rayuwarshi, wacce ta cire shi daga wahala ta bashi so da kauna ta raine shi fiye da yadda ta raini 'ya'yan da ta haifa da cikinta, ko gaisuwa aka mishi sai dai ya gyaɗa kai don baya magana, idanunshi har tsoro yake ba wa wasu idan ya buɗe, An yi an yi ya ci wani abu tun safen har dare ko ruwa bai yarda ya sha ba don raɗaɗin da yake ji daga zuciyarshi har akan harshen shi baya tunanin zai iya cin wani abin don cikin nashi ma jinshi yake a cushe, ganin yana shirin yi wa kanshi illa ya sa Sulaiman yi mishi allurar bacci don daga ƙarshe numfashi wahalar fita ya fara mishi. Su basa yarda da wani zaman makoki daga yinin da aka binnetan duk na waje suka watse, Afeefah tsabar yadda ta kasa yarda cewa Mammi ta tafi a ɗaki ta cigaba da zama hakan ya mata hijabi da haduwa da mutane dayawa ciki har da su mommy da Saleem, don Saleem yayi niyyan kwana a tare da Rayyan mommy ta sanar dashi yayi aure ai, ya shiga tsantsar mamaki ya kuma ji babu daaɗi a lokaci guda, yana mamakin yadda Rayyan yayi aure cikin kankanin lokaci alhali shi bai taɓa ji Rayyan ya furta sunan wata macen a matsayin buduruwa ba, ya kuma ji ba daaɗi yadda bai kasance tare dashi a bikin ba amma ya mishi Fatan alkhairi ya ɗauki su mommy suka koma gida don har yanzu a tsohon gidansu suke har shi, ya ce ba zasu koma chan inda ya zauna da Sabrina ba wani zai saya musu don bai san me suka binne ciki ba. sai dare ta fito ta nufi ɗakin Abeeha dake kwance rib da zazzabi, a gangarta ta zauna tare da rike hannunta "Afeefah da gaske Mammi ta tafi ko? Idan na je ɗakinta ba zan ganta ba ko? Yanzu shikenan ba mu da uwa ba mu da uba?" Ta danne hawayen da ke shirin ziraro mata tace "Haka Allah yake lamarinshi Adda Abeeha, dukkan mu da muke rayuwa a yanzu kwananmu ne bai kare ba idan ya ƙare dole za mu tafi" "ba za ki gane raɗadin da nake ji ba Afeefah" Ta girgiza kai "Duk wanda za ki ji Adda Abeeha na ji shi, kar ki manta ko da aka haifeni ba ni da uba, ban kuma buɗi ido na tarar da mahaifiyata ba sai a hoto kin ga ko zafi da raɗaɗin maraici na fara dandana, shi ne tun a cikin cikin mahaifiyata har zuwa zanin goyona. Adda Abeeha ku gode Allah kun rayu da iyayenku har girman ku..." Kuka ne ke shirin kwace mata amma ta dake ta danne. "Don Allah ki daure ki daina yi wa Mammi kuka haka! Mu bita da Adu'a shi ta fi buƙata a halin yanzu" Matar uncle Sanusi dake ɗakin tace "maganar Afeefah gaskiya ce Mahaifiyarku Adu'a take buƙata Abeeha ba kuka ba ita ai tata ta yi kyau! Allah ya sa jinyar da ta sha ya zama kankarar zunubanta ne" Suka amsa da Ameen. "Mommy ya Adda Jannah?" Afeefah tayi tambayar a sanyaye. Matar uncle sanusi tace "Ta farka amma tana under kulawar likitoci don ɓarin ya zo ne bagatatan ga cikin ya fara girma, ta dai ji jiki kam sai dai Allah ya kawo na moro suna chan tare da su mamanku" Ta fahimci da su matar uncle Mansur take nufi don haka Adu'a suka mata na samun ingantacciyar lafiya. Abeeha ta dubi Afeefah "Yaya fa?" Shiru Afeefah tayi don bata san me zata ce ba, a lokacin mommyn ta fita daga ɗakin "Yana ɗakinshi Adda Abeeha" Miƙewa zaune Abeeha tayi ta riƙo hannunta. "Afeefah na san zaman ku da yaya babu daaɗi, na kuma san kina tsoron shi da kuma tsoron kasancewa inuwa ɗaya da shi amma wallahi a yanzu babu wanda Yaya zai fi buƙata kaman ke! Mammi za ta yi farin ciki idan kika kular mata da shi at his worst moment irin wannan..." "Ta yaya Adda Abeeha? Mutumin da bai taɓa min kallon matsayin abu mai muhimmanci ba, wanda bai taɓa ɗaukata da kima ko daraja ta mace ba macen ma matarshi?" Tayi maganan cikin sanyi, tun ɗazu yaƙi take da zuciyarta akan Rayyan, tana so ta je inda yake amma tana tsoro ta san yana buƙatar wani amma bata san ta yadda za ta rarrashi mutum irin shi mai dakakkiyar zuciyar da baya bayyana rauninshi a fili ba. "Trust me Afeefah za ki iya, na san kema kin san me ya fi buƙata a yanzu tunda duk waennan abu kin yi going through a rayuwarki... A lokacin da muka rasa Abbu akwai Mammi Dukda bata da lafiya ta tsaya mana dukkanmu har saida muka zama daidai muka amshi ƙaddararmu amma a yanzu bata nan ita da ta fi kowa sanin Ya Rayyan a duniya, na sani a kwanakin nan bacci sai dai idan da allura ko magani hakanan zai yi ta ciwo amma ba zai nuna ba, ba zai yi magana ba ba zai ci abinci ba don Allah ki taimakemu ki kula dashi matsayin ki na matarshi" Kai Afeefah ta gyaɗa ganin Abeehar ta fara hawaye, tun dazu take so taje gareshi har cikin zuciyarta amma bata san me zata yi ba in taje ɗin, Miƙewa tayi tana kallon Abeeha "Ki yi bacci zan kula da komai in shaa Allah" Godiya Abeeha zata yi mata amma tayi saurin ficewa Abeeha ta mayar da idanun ta rufe hawayenta na gangara. Afeefah na barin sashen tayi ɗakin ta wanka tayi saboda yanayin zafi da ake dan yi tayi Sallar isha ta jima tana yiwa Mammi Adu'a tana hawaye kan ta yi shafa'i da wutiri ta nemi riga da wando na bacci jajaye ta saka ta ɗora hijab har ƙasa a kai sai ta fito ta nufi ɗakinshi, sai da tayi knocking ta buɗe ta shiga hasken a kunne don haka ta hange shi kwance kan gadon ɗakin idanunshi a rufe ya ɗan dukunkune kaman mai jin sanyi amma kuma bai rufa ba, kamshin shi da ya kama ɗakin na nan yadda yake ta nufi gaban gadon ta ɗan tsaya a kanshi kaɗan tana kallonshi. Allah sarki mutuwa, in ba mutuwa ba mai ya isa ya jijjiga Rayyan har haka a yini guda har ya rame, fuskarshi dake fari tass yayi wani irin ja musamman kan hancinshi, daga yanayin baccin da yake zaka san ba na farin ciki bane don a baccin ma sai yamutsa fuska yake, a hankali ta ja bargon ta lulluɓa mishi har kafada, sai ta isa wardrobe dinshi ta dubi wani bargo ta zo ta shimfida a ƙasa ta zagaya ɗaya ɓangaren ta ɗauki pillow daya dake cike da kamshinshi zuciyarta na bugawa sossai ta kwanta a ƙasan bayan ta kashe wutan ɗakin, ko motsi tayi sai taji kaman yana nan a kusa da ita saboda yadda daga bargon har pillown ke fidda azabbaen kamshin shi ga kasancewar ta under roof ɗaya da namiji abin da bata taɓa ba sai take jin ta wani iri da kyar bacci ya ɗauketa. Chan cikin dare sai ta fara jin kaman numfarfashi a ɗan tsorace ta farka ta miƙe zaune sai ta ji kaman daga kan gadon da yake kwance ne da sauri ta miƙe tsaye ta tafi ta kunna hasken ɗakin ta nufi gangar shi. Ya haɗa zufa yayi sharkaf sai juye juye yake kaman mai mummunan mafarki, numfashinshi na seizing kaman mai ciwon asthma hankalinta ne ya tashi bata san ta riƙe hannunshi ba tana jijjigawa "Ya Saraki! Ya Saraki ka tashi..!" Duk ta ruɗe saboda yadda yake yin kaman zai mutu, da karfin gaske ta jijjigashi hakan ya sa ya buɗe rinannun idanunsa ya zuba mata yana sauke numfashi a hankali hankali, hawaye ne ke bin idanunta suna diga a duk inda suka samu zarafi kama daga gaban hijabinta har kan hannunshi dake cikin nata. "Mummunan mafarki kake? Sannu ka ji? Bari na kawo maka ruwa" Duk ta rikice tsabar yadda ta ganshin ya dameta, da sauri ta nufi frigde ta kawo mishi ruwa da kyar ya miƙe zaune ya ɗan yi tapping wayanshi ya kalli time karfe biyu, lumshe ido yayi ya buɗe a kanta tana miƙa mishi ruwan, bai san me yasa ya karɓa ba ya dai tsinci kanshi yana shan ruwan yana jin wani abu dake tsaye mishi a makoshi na sauƙa a hankali, sai kuma ya ji cikinshi na murdawa yana jin amai na taso mishi rabon shi da abinci tun jiya da daddare don ko karyawa bai yi ba rashin lafiyar mami ya riskeshi, ruwan ya miƙa mata tana daga tsaye tana kallonshi har lokacin idanunta na cike da kwalla. Ƙoƙarin sauƙa yake daga gadon ba tare da ya ce uffan ba sai jiri ya kwashe shi ya tafi zai faɗi da wani irin hanzari ta riƙe shi "Ya Saraki baka da lafiya...! Jikinka zafi sossai me kake so in kawo maka?" A karye take maganan, kaman ba zai yi magana ba yana tsaye tana dafe dashi Dukda ya tabbatar in faɗuwar ne ɗan tiny body ɗintan nan bai isa riƙe shi ba a hankali yace "Amai...!" Kalma na farko da ya furta kenan tun bayan Ameen da yake ta cewa in an yiwa Mammi Adu'a. "Amai za ka yi? Sannu mu je bayin ko in kawo maka abu ka yi daga nan?" Shiru ya mata sai ya yunkura zai cigaba da tafiya nan ta gane bayin yake son zuwa da taimakonta ana tafiya ana hutawa suka shiga bayin, sai da ya dafe jikin sink ya kalleta ya kalli kofa. "In fita? Za ka iya?" In ba don halin da yake ciki ba za ta iya rantsewa ya Harare ta, bata ƙara magana ba ganin ya zuba mata idon da suke sake firgitata da bata tsoro ta fice da sauri sai da ta rufe kofa ya lumshe ido. Kai tsaye kitchen nasu taje ta haɗo tea mai kauri ta dawo ɗakin gadon da ya jajjanye bedsheets ɗin ta gyara ta tsaya daga gefe kaman security, ganin ya jima bai fito ba ta yunkura ta nufi bayin tana shirin yin knocking yana buɗe kofan da sauri ta matsa baya, ya kalleta ya dauke kai ganin bashi da ƙarfin jiki ta matso ta kama hannunshi bai hanata ba har suka isa kan couch ya zauna yana jinguwa tare da riƙe kanshi da kaman zai fashe yana cewa "Asshhhh!" Kaman zata yi kuka take jera mishi sannu. Tea din ta ɗauko "Ya... Saraki!" Ta faɗa a rarrabe, ya ɗan buɗe ido ya kalleta yana jin sunan na mishi wani iri har a cikin jikinshi "ka sha tea ka ga cikin ka babu komai sai ka sha magani Don Allah..." Ya lumshe ido kawai fuskar nan tamau, hawaye ne ya zuba mata ta ɗan ja Shesheka sai ya bude idanun yana kallonta ya zubawa hawayen idanu haushi yake ji, takaici yake ji Meyasa shi ba zai yi kukan kaman kowa ba? Meyasa take da arhar hawaye a sadda shi yake nema? Zuciyarshi zafi yake mishi raɗaɗi da kuna yake mishi. Hannu ya miƙa mata don yana da buƙatar yin Sallar isha don bai yi ba kuma ba zai iya samun karfi ba matukar ba abu bane ya shiga cikinshi, da sauri ta miƙa mishi ta koma gefe tana share fuskanta wanda ta rasa me yasa hawayen nata suka ki tsayuwa muddin ta kalleshi sai ta ji suna zubowa tsabar tausayinshi. Kurba bai fi hudu yayi ba ya ajiye, ta dubo magungunanshi ta ajiye mishi ya kalleta tace "Don Allah Ya Saraki ka sha ko zaka samu sassauci...!" A karye tayi maganan yayi shiru "Wanne ne zan cire maka?" Ya sake yin shiru "Ya Saraki...!" "Get out of this room..!" Yayi maganan a kausashe ta girgiza kai za tayi magana ya ce "Nowww!" Da ƙarfi yayi magana yana zaro mata idanu... 🖤Gureenjoh🖤 HAIHUWA DA HANJI (A True life story) Fatima Muhammad Gurin (Gureenjoh) Wattpad-Gureenjo6763 Arewabooks-Gureenjoh ADABI WRITERS ASSOCIATION *FREE BOOK* *39* Kuka ta sakar mishi mai sauti ya kawo idanu ya zuba mata yana mamaki a ƙasan ranshi, ganin ta ƙi fita ya sa bai bi ta kanta ba ya ɗauki maganin ya hadiye ya tura mata taje ta ɗauka ta mayar inda ta samu ta sake ja ta tsaya, Miƙewa yayi ya isa wurin Sallarshi ya tada sallah. Bayinshi ta shiga itama tayi Alwala ko kan ta fito ya idar da isha nafilfili yake yi itama ta fara nafilfilin sai uku da wani abu taji ta gaji shima yana zaune ne kanshi da yake jin kaman zai fashe jingine da jikin gado, Miƙewa tayi taje ta kwanta a inda ta kwanta da farko nan ƙasa tana kallonshi zuciyarta cike da tarin tsantsar tausayinshi tana kuma mamakin irin karfin halin da tayi har bacci ya sureta bata sani ba. Karfe biyar da rabi ya buɗe idanunshi ya miƙe yaje yayi alwala, har ya wuce ta kaman yayi fitanshi ya kyaleta sai ya tuna irin kulawar da ta bashi a daren na jiya da irin yadda tayi ta zubar da hawaye akan damuwarshi, ko da Abeeha ce ba zai barta ana sallah tana bacci ba, tsugunawa yayi don bashi da wani ƙarfin magana ya sa hannu ya ɗan ja hijab ɗinta firgigit tayi ta tashi tana kallonshi don baccin dama rabi da rabi ne inda bata saba ba, Miƙewa kawai yayi ya fice bai ce komai ba. Da sauri ta miƙe taje ta yi Alwala ta zo ta gabatar da sallah, bata tsaya doguwar Adu'a sossai ba ta miƙe ta gyara ɗakin tsaf ta share ta saka turaren wuta kan ta fice zuwa babban kitchen, duk abincin da aka ci jiya a wurin makoki order ne daga manyan restuarants yau kuma a gidan za'a girka don haka tana bukatar ganin me zasu yi Dukda ba wasu mutane ne na waje ba kadan da suka Kwana duk na gida ne. Pepper soup ne na cowtail da bread sai tea da suke zubawa flasks flasks daga nan ta wuce wurin Abeeha ta samu idanunta biyu suka gaisa take tambayarta jikinta ko da Abeeha ta tambayi "Ya Yaya Rayyan?" Bata wani damu ba ta ce "Ya fita masallaci" Murmushi Abeehar tayi ɗan kaɗan Allah sarki ta je ta kulan dashi kenan. Shi kam daga masallaci mota ya ɗauka ya fice asibiti su jannah sai ganinshi suka yi, da sauri ta sauƙo ta zo ta riƙe shi zata fara kuka ya rabata da jikinshi ya ja hannunta zuwa bakin gadon ta zauna. "Menene na kukan? Uhmm? Lafiyar ki ya kamata ki yi focusing a kai mun riga mun yi rashi, haƙuri kuma ya zame mana dole ki bar kukan nan" Kai ta gyaɗa tana share hawayen dake silalo mata, bata jin tausayinsu kaman yadda take jin nashi don yana maganan ne kana jin yadda ɗaci dake shimfide bisa zuciyarshi ke hauro wa har kan harshen shi. Ya gaishe da matar uncle Mansur dake ɗakin ɗayar cousin ɗinsu ya gaishe shi ya amsa suna ƙara yi mishi gaisuwa. Sai da yaje wurin bills aka tabbatar mishi mijinta ya biya komai ya dawo ya nemi da su zo su koma gida tunda ta ji sauƙi, tattara wa suka yi ya ɗauko su har gida ya shiga ciki ya duba Abeeha a lokacin Afeefah bata nan, ko da zasu fara kuka ganin juna faɗa ya hau su dashi dole suka yi shiru ya gaisa da iyayen da suke ciki kan ya miƙe ya nufi sashensu har lokacin kuma kanshi kaman zai rabe amma juriyarshi ya hana shi kwanciya. A tsakiyar parlorn suka haɗu ta fito daga ɗakinta sanye da doguwar riga mai faɗi sai karamin hijab da ya shiga da kayan, ganin shi ya sa ta dake tare da danne tsoron ta ta furta "Ina kwana Ya Saraki? Ya jikin?" Da ɗan hanzari tayi maganan ganin zai wuceta. "Lafiya" Ya amsa kan ya wuce ya shige ɗaki, zama tayi don ta san kila yanzu wanka zai yi sai da ta ɗauki awa kan ta miƙe ta nufi dining ta haɗa mishi tean ta ɗauki bowl ta dibi pepper soup ɗin ta haɗa a karamin tray ta nufi ɗakin, ya yi wanka manyan kaya ne a jikinshi kaftan baƙar yadi mai taushi da ya sake fito da ainihin hasken fatar shi sannan ramarshi ma ya bayyana, a kan couch yake zaune yanzu ma yayi relaxing sossai idanunshi a rufe, waya ya gama yi da likitarshi bata nan ta samu labarin rasuwa hankalinta ya tashi roƙon shi take akan ya samu ya zubar da hawaye yayi leting damuwarshi fita ko kaɗan ne in ba haka zai iya samun matsala ya dai mata shiru ne amma bai san ko zai iya ba yana son yin shima ko zai samu sassauci amma taurin ranshi na dayawa, kuma hakan na da alaƙa da training da ya samu a farkon rayuwarshi. Shigowar ta bai sa ya buɗe idanu ba har ta ja ɗan table ta ajiye mishi tray ɗin ta tsuguna "Ya Saraki..!" Har ranshi ya ji sunan, bai san Meyasa duk ta kirashi hakan sai ya ji kaman an kirashi ba kuma dole zuciyarshi take motsawa ta wani ɓangaren kuma sai yaji kaman Mammi ce ta ƙira shi, dole ta sa ya buɗe idanu ya kalleta ta sauƙe nata ƙasa don ba zata iya jurar kallon cikin idanunshi ba ko a yana ƙalau ma bare yanzu da suke a birkice. "Ga abin kari nan na kawo maka, Don Allah ka ci ka samu ka sha magani." Idan dutse ya tanka to ya tanka, jin shirun yayi yawa ta ɗaga ido ta kalleshi yana lumshe da idanun abin shi. "Don Allah dai ka ci Ya Saraki! Ko babu daaɗi ka lallaɓa ka ci ko kaɗan ne a yanzu ba mu da wani majingina bayan kai, ko da ni bana buƙatarka su Adda Abeeha suna da buƙatarka bare ma dukkanmu kaine bangon mu a yanzu ba za mu so ganin komai ya same ka ba a wannan gaɓar da bamu warke raunin tafiyar Mammi daga rayuwar mu ba.." Muryarta ya shiga rawa hawaye ya shiga silalo mata. Sunan Allah yake ƙira a hankali "Ya Allahu!" Kalaman sun dirar mishi da wani rauni da baya tunanin ya taɓa jin irin raunin zuciyarshi na rawa sossai, yadda ta furta cikin kuka ya sa yaji idanunshi kaman za su iya kawo ruwa muddin ta cigaba da irin waennan kalaman cikin sanyin murya da Salon karya zuciya. "Ki je zan ci!" Ya faɗa a hankali, bazata taji kalaman kuma hakan ya sakata jin daaɗi tunda ya yarda zai ci ta miƙe ta kawo mishi magungunan shi kusa kan ta fice sai da ta fita ya buɗe idanu ya zubawa kofan da ta rufe sama da seconds goma kan ya ɗauke ya mayar kan abincin, ya kuwa sha pepper soup ɗin mai yawa ya sha tean tare da magani ya ajiye ya miƙe ya koma kan gado ya kwanta don jiri yake gani a cikin maganin akwai na saka bacci ko da bai so ba dole baccin ya ɗauke shi dama ya saba ko da zai sha da daddare baya iya bacci amma in da rana ne yana yi ba tare da mugun mafarkin shi ba. **** "Malam Labaran Haƙƙin uba zuwa ga 'ya'yansa yana da matuƙar muhimmanci musamman a musulunce, wannan haƙƙi yana tattare da nauyin kulawa, tarbiya da tabbatar da rayuwa ta gari ga 'ya'ya ciki sun haɗa da: Samar da halal ɗin haihuwa wannan ba sai na yi dogon jawabi ba na san ka fahimta ya kasance an samu wannan yaro ta hanyar aure kaman yadda addini ya tanadar. Alhakin samarwa yaro suna mai kyau da ma'ana wadda bai sabawa Addini ba. Ciyarwa da sutura uba na da nauyin ciyar da 'ya'yansa da matansa daidai gwargwadon iko, hakanan da saya musu sutura da tufafi daidai gwargwado. Ga babban wato ilimi da tarbiya, koyar dasu abubuwan ibada sallah, azumi da sauransu. Samar musu da ilimin zamani da horo da zai sa su zama masu amfanar da kansu da al'umma. Ka ga tarbiya a kan hali ba karamin alfanu yake da shi ga yaranmu ba dole ne akanka ka basu horo a kan gaskiya, amana, girmama manya da kyakyawar mu'amala da mutane. Suna da alhaki akanka na basu kariya da tsaro hakan ya haɗa da hana su mu'amala da miyagun abokai ko dabi'u kaman su shaye-shaye, fasikanci da sauran su. Malam Labaran uba kan zama abin koyi ga ɗa wajen addini, hali da mu'amala ina so ka yi nazari a iya tunanin ka matsayinka na uba kuma miji me ka sauƙe a cikin waennan?" Inna Larai ta numfashi "Wallahi malam liman ina ga bayan hakkin farko na samar da su ta hanyar aure babu abin da Malam Labaran ya sauƙe ciki ko haihuwa aka yi mutumin nan baya ragon suna." Inna Asabe da kanta ke ƙasa tace "Mun samu tawaya sossai saboda rashin ilimi da rashin sani gashi mun lalata rayuwar 'ya'yanmu" Malam Labaran yayi shiru jikinshi a sanyaye kenan shi fa Allah zai kama da laifi? A hankali yace "Toh malam liman wani hanya za mu bi mu gyara abin da muka ɓata tun farko? Hakikanin gaskiya ina samun abin da zan iya rufawa kaina asiri da gidana amma son zuciyata ya sa nake kyashin sayowa in kawo, kowa ta kanshi yake kaman rayuwar bariki hatta sutura wannan na manta rabon da in saya ma kowa a gidan, Dukda ina kallonsu da suturu da ma wasu ababen ƙawa amma ban taɓa tambayar ina suka samu ba sai ma fata nake in ga nasu in kwace ko in sace...kaico kaico da wannan rayuwar jahilcin" Hawaye ne ya zubo mishi don sai a yanzu yake fahimtar irin illar da jahilci yake dashi, ga yaran duk sun lalace ya tabbatar babu mai auren su a tunaninsu Afeefah ce ba zata auru ba saboda yadda tayi tambari a garin sai gashi ta auri wanda kaf kauyen basu da kamarsa, haƙiƙa yayi matukar nadamar abubuwan da yayi tayi a baya na tsantsar rashin ilimi. "Hanya ɗaya ne jal kuna raye lokaci bai ƙure ba, ayi Adu'a a nemi yafiyar waenda aka zalunta babban hanyar shine a nemi sani akan addini." Nasiha ya cigaba da yi musu mai ratsa jiki sai gashi duk jikinsu yayi wani irin sanyi, inna Larai dake fama da azabar kafa kawai ta kama kuka, lallai Allah mai girma ne kuma baya abu kan kuskure hassada da bakin ciki akan rayuwar Afeefah ya ja ta jefa kanta da kanta ga halaka. Anan aka saka kawu Labaran mayar dasu dakunansu, inda ya nemi zai dinga zuwa daukar karatu masallacin da malam liman ke koyawa kowani bayan Magrib haka zai yi kokari ya ga ya sauke duk wani hakkinshi amma bai san inda zai ga Afeefah ba. "Za ta zo ne! Dole zata neme ku don ku ne dolenta" Kanshi ya duƙar ba tare da ya yarda da zata zo ɗin ba don su kaɗai suka san irin cutarwan da suka yi mata. **** Samha ce zaune da Abeeha bayan Magrib tana ɗan janta da hira yayinda jannah ke kwance akan gado idanunta a lumshe Afeefah tayi sallama ta shigo ɗakin. Idanu suka hada da Samha, sai tayi kaman bata santa ba ta ɗauke kai ta nufi wurin jannah "Addah jannah sannu, ya jikin? Akwai abin da kike bukata ne?" Ta girgiza kai "Babu, bacci ma zan yi yanzu ki huta da zirga-zirgan nan haka please tun safe kece nan ke ce chan baki huta ba" Afeefah ta ɗan murmusa kadan Dukda ta gajin iya gajiya rabon da tayi irin wannan wahalar ma tun Dutsen-wai, ita ce kitchen ita ce kaiwa mutane abinci da sauran dai duk wani zirga-zirga da za'a rike mutum a gida a yayin hidima ko ta aure ko ta mutuwa. "Shikenan Addah jannah, Allah ya kara sauƙi... Adda Abee Allah ya bamu alkhairi wanka zan yi na kwanta" "A huta gajiya Afeefah sannu" Tayi murmushi kawai ta juya ta fita. Samha da ta zuba mata idanu tun shigowarta gabanta na wani irin faɗuwa tana sake kallon irin sauyawar da tayi da kyaun da tayi ga kamshi kaman wacce ta tsumu ta tashi cikin arziki ta miƙe tsaye tana kallon Abeeha "A..Abeeha wanchan ba Afeefah ba?" "Kin santa ne?" Abeeha tayi tambayar kaman bata san labarin komai ba. "Afeefah Afeefah...!" Sai ta rasa wani kwatance zata yi da Abeeha zata gane "Afeefah dai wacce ta fito daga wani kauye wai shi Dutsen-wai?" Abeeha tace "kila kama dai, wannan Afeefar kaman sister take a wurin mu kuma ita ce matar Yaya Rayyan" Wani irin kallo Samha ke mata zuciyarta na bugawa da ƙarfi ko a mafarki ta ganta zata gane ta, Afeefah ce ta koma haka? Wait Afeefah ce take auren Rayyan? Rayyan fa! Kwakwalwarta ya kasa ɗaukar wannan zance za ta yi magana Sameera ta shigo "Samha mu tafi tun dazu Yaya Saleem ke faɗan mun ajiye shi" Bata tsaya jiranta ba ta fice, Abeeha tace "Ki je kar yayi faɗa, mun gode sossai fah sai da safe" Ta ɗauki Jakarta ta fice zuciyarta fal mamaki da saƙe-sake to ko bata gane Afeefar bane? Kai dole in sun zo gobe ta nunawa mommy da su Sameera ita ko ita ce bata gani da kyau ba haka ta danne maganan ta kasa yi da kowa har suka bar gidan zuwa gidansu akan gobe ma zasu shigo. Ita kam Afeefah ko tsayawa tunaninsu bata yi ba dama damuwarta Saleem ne kuma fahimtar ya dawo daidai hankalinta ya kwanta don haka bata da wani issue da su, wanka tayi ta nemi cotton peach kayan bacci riga da wando dogo ta saka sai da tayi isha ta yi shafa'i da wutiri ta miƙe ta kashe komai na ɗakin ta ɗauki wayanta ta fito gabanta na faɗuwa, rabon da su hadu tun safe da ta bashi abin kari don da rana yana parlorn waje da su Saleem so a chan aka kai musu abinci basu haɗu ba, bata san ma ko ya ci ko bai ci ba haka dai ta nufi ɗakin tayi knocking tare da tura kofa ta shiga, kallon wurin yayi sai suka haɗa idanu yana zaune akan gadon kafafunshi biyu na cikin bargo bayanshi na jingine da pillow ramarshi ya sake fita ainun. Ɗauke kai yayi chan ƙasan ranshi yana mamakin yadda a yanzu take shigo mishi ɗaki don tsabar neman magana ya kore ta kuma ta mishi kuka bai sani ba ko tare aka gina musu ɗakin ne oho, abin da ke damunshi ya dameshi don haka bai kula ta ba har ta ɗauko bargo ta shimfida inda ta shimfida jiya taje ta ɗauko pillow ta zo ta ajiye sai ta matsa kusa dashi "Ya Saraki sannu! Ya jikin? Kana bukatar wani abu ne?" Ya buɗe ido ya kalleta ta ɗauke kai kaman ba zai amsa ba sai taji ya ce "Da sauƙi" Daga haka bai sake magana ba taje ta ɗauko ruwa ta zo ta ajiye a bedside ko zai buƙata, wayanshi ta gani a kan couch taje ta ɗauko tazo ta ajiye mishi gefen ruwan kan taje ta kashe wutan ta zo ta kwanta ta bar shi da mamakin ƙarfin hali irin nata... 🖤Gureenjoh🖤 HAIHUWA DA HANJI (A True life story) Fatima Muhammad Gurin (Gureenjoh) Wattpad-Gureenjo6763 Arewabooks-Gureenjoh ADABI WRITERS ASSOCIATION *FREE BOOK* *Ina Editing ashe ban gama ba bacci ya ɗauke ni. Ku karya da wannan* *40* Ya jima zaune yana kallon figure ɗinta cikin duhun ɗakin kan ya zame ya kai kwance yana sanya pillow a kirjinshi, idanunshi a lumshe sama da awannin da ba zai iya lissafawa ba har bacci ya ɗauke shi a haka ɗin, chan cikin baccin shi ya fara jin abin da yake ji muddin ya rufe idanu da sunan baccin dare ji yake kaman zai mutu, kaman an saka abu ne aka danne mishi kirji numfashinshi ya toshe juye juye yake ya haɗa zufa sharkaf sai numfarfashi yake fitarwa sama sama. Cikin baccinta ta soma jinshi a hankali ta buɗe idanu sai dai jin yadda yake yin yasa bata san ta miƙe ba taje ta kunna wuta gabanta na faɗuwa ganin kaman zai faɗo daga kan gadon ta ƙarasa wurinshi da gudu tana jijjiga shi Muryarta na shaking take ƙiran sunanshi "Ya...ya Saraki! Ya Saraki...! Ka buɗe ido.. Ka tashi ya Saraki mafarki ne... Don Allah ka bude ido...innalillahi!" Duk ta rikice ta ruɗe sai dai kaman bai san tana yi ba har lokacin idanunshi a rufe suke yana jan numfashi da kyar, kuka ta saki tana janyo wayanshi ta shiga neman Layin likitarshi jikinta na tsuma saboda tashin hankali, kiranta tayi Allah ya taimaka ya kusa yankewa ta ɗaga "Dr. Yaya Saraki ne... Ban san me zan mishi ba ya ƙi tashi sai juye juye yake kaman zai mutu ki taimakeni..!" Likitan da take sensing tashin hankali a Muryar Afeefah tausayinsu duk ya rufeta ta ce "Ki natsu Afeefah natsu! Faɗa min me yake yi?" Kaman za ta taya shi kokawa da numfashi ta shiga cewa "juye juye yake yi, ya jiƙe sharkar da zufa, he's just gasping for air kaman baya iya isar da numfashi inda ya kamata jikinshi rawa yake.." "Ki ji Afeefah Rayyan na gab da shiga cikin mummunan yanayin matsalar kwakwalwa idan baki taimakemu ba, ki taimaka ki san yadda zaki yi ki saka shi yayi kuka ya zub da hawaye in ba haka ba akwai matsala..." Wasu tips ta bata tare da yanke wayan akan dole gobe da safe su tafi asibiti he cannot continue like that. Jefar da wayan tayi a kan gadon ta tattare ƙarfinta gabaɗaya ta ɗago shi ta jijjigashi da karfin gaske tana ambatar sunanshi sai ya ja numfashi mai tsawo yana buɗe idanu amma sai idanun su tafi luuu kaman za su rufu idan ta sake ƙira sai su buɗu sun yi wani irin ja da sauri ta kafa gwiwowinta akan gadon ta zare hijabinta ta jefar tare da ma kanshi ta mishi kyakyawar masauki a kan kirjinta ta rungumeshi Tsam tana kuka sossai, yadda ta yi hugging nashi, yadda take shafa kanshi da duk hannayenta biyu zuwa wuyanshi yadda take kara matse shi, sautin fitan muryarta cikin kuka ya sa bai san sadda ya mayar da hannayenshi jikinta ba ya rungumeta ƙamƙam... Cikin sautin kuka take furta "Ya Saraki ka sassautawa zuciyarka don Allah, wannan wahalar yayi maka yawa don Allah ka daure ka zub da hawaye ko kaɗan ne... Zan zama kurma daga jin sautin Muryar fitar damuwarka! Zan zama makauniya daga kallon ruwan hawayenka! Kwakwalwana zai shiga ɗimuwa har lokacin nan ya zama tamkar mafarki ko dilusion a gareni just cry ka ji? Ka yi kuka ba zan ji muryarka ba i promise...Muna mu...na son lafiyarka we will always be there for you... Ka yi kuka just let your worries our this will be our Lil secret ka ji?" Har lokacin bata daina shafa suman kanshi ba cikin wani irin kulawa, sake ƙamƙameta yayi kaman zai ɓallata jikinshi na sake ɗaukar rawa zuciyarshi na wani irin tsitsinkewa Dukda irin yadda take ji da zafi dake ratsa ta haka ta sake hugging nashi, she hugged him until his soul melts into tears sai ji tayi yana sauke wani irin numfashi mai tafe da zafafan hawaye masu rikitarwa. Lips ɗinta ta datse tana runtse ido a sadda sautin shi ke shiga cikin kunnuwanta a hankali yana samun masauki a cikin zuciyarta, bata daina shafa shi ba shi kuma bai daina sake kankanmeta ba ya fi mintuna talatin cikin wannan yanayi kan a hankali ya fara sassauta riƙon, gefe gefe tayi ta kwanta yayinda ya bita har lokacin kanshi na kan chest ɗinta dake beating so so fast tana shafa shi da hannunta tana jin jikinshi na sauyawa daga zufa zuwa zafi dake shiga har cikin jikinta, sai da suka kai kwance ta iya jin ruwan hawayen shi na sauka a kan silk maroon rigan baccinta Yana taɓa fatarta ta runtse ido kawai. Basu san iya adadin lokutan da suka ɗauka a hakan ba har bacci ya ɗauke shi itama baccin tayi. Ƙarfe biyu da wani abu ya sake farkawa, shiru yayi yana shakar fitinannen kamshinta yana jin hannayenta a jikinshi, ɗaya a cikin tattausan gashin kansa ɗaya a bayan wuyanshi, a hankali ya zame ya miƙe zaune wutan ɗakin a kunne har lokacin amma ba tarrr ba mai ɗan duhun yana iya kallon fuskarta a haka, idanu ya zuba mata yana aikin kallo her caramel skin, dogin lashes ɗinta pointed nose ɗinta zuwa thin beautiful lips ɗinta he just felt lost a kallon nata moments ɗinsu na ɗazu na dawo mishi kaman yanzu, he can't believe that it happened. It really happened! he cried in this little Girl's arms, the way she caresses him, pet him like a Lil boy ya tsaya mishi sossai a rai. Sauƙa yayi daga gadon ya ja duvet ɗin ya rufeta zuwa kirji sai ta ɗan gyara kwanciya kaman dama a takure take ya shiga toilet yana jin wannan nauyin na cikin zuciyarshi ya ragu, ruwa ya kunnawa kanshi ya jima a ciki har lokacin kuma duk motsinshi kallon kanshi yake akan chest ɗinta tana bashi utmost kulawa, wanka yayi ya fita ya zo ya nemi jallabiya ya saka ya fara nafilfili har sai da ya ji zazzabi na neman fin karfinshi ya miƙe ya zare jallabiyar ya saura daga shi sai guntun wando da karamar vest da ya bayyana duk wani kakkarfar sura mai cike da zati da Allah ya mishi gadon ya hau ya ja bargon shima ya ɗan rufa tare da juyawa ya zubawa face ɗinta idanu tana baccinta peacefully har bacci ya sake sace shi a haka. Ita ta fara farkawa da asuba ta sauke idanunta akan kyakyawar fuskarshi, ta ɗan jima tana kallonshi kwakwalwarta na tuna mata abin da ya faru a daren, nauyi da kunyarshi suka lallaɓo suka rufeta amma ta kasa ɗauke idanu daga kallonshi he's just handsome so so handsome da bata san ya zata kwatanta shi ba, yana baccin kaman ba shi bane Saraki mai zuciya a kusa, wannan masifaffen marar fara'a da son Magana murmushi ta tsinci kanta da yi Alhamdulillah atleast ta samu riba a kanshi wani abin dole ta san ya ragu mishi hakan kaɗai ya faranta mata, sauƙa tayi daga gadon tare da ɗaukan hijabinta ta saka ta shiga toilet don yin alwala tana jin ko me ta mishi bata ragu ta kowani fanni ba saboda he's her life savior ba don shi ɗin ba da yanzu tana cikin matattu matattun ma cikin sahun masu gingimemen laifi wa ubangijinta. Tana rufe kofan bayin ya buɗe idanu sai dai bai motsa ba don zazzabi ne sossai a jikinshi har numfashin da yake fesarwa na fitar da zafin hucin zazzabin, bayan tayi alwala ta taho gadon ta taɓa goshinshi sai taji shi rau a hankali ta shiga kiran sunanshi "Ya Saraki..! Ya Saraki...!!" Ya rasa wani irin effect sunan ke dashi a zuciyarshi don wani irin tsalle zuciyar tashi tayi a sadda ta ƙira sunan cikin tsiririyar muryarta Idanu ya buɗe ya kalleta "Sannu! Na ji jikinka zafi sossai za ka iya tashi ka yi sallah? Ko in idar in kawo maka ruwan nan?" Idanunta kawai yake kallo hakan ya sa ta kawar da idanun yace a hankali "Zan iya" Daga haka ta koma baya ta tada sallah kar ya ga kaman ta cika zaƙewa, shi kuwa ya ɗan jima a haka kan ya yunkura ya miƙe zaune yana dafe kanshi, a hankali yake tafiya har ya isa bayi yayi alwala ya dawo sai ya kasa Sallar a tsaye duk kafin halinshi a zaune ya gabatar bayan ya idar ya miƙe ya koma gadon tare da lullubuwa, bayan ta idar ta miƙe ta ninke sallayar tana shirin fita wayanshi ya ɗauki ƙara sai ta koma taje ta ɗauka ganin Likitarshi yasa ta ɗaga suka gaisa take tambayarta ya ya kwana nan ta mata bayanin zazzabi ne a jikinshi sossai Dukda ya samu ya zub da hawayen. Hamdala tayi da farko kan tace za ta turo yanzu collegue ɗinta zai zo ya saka mishi drip da wasu allurai in shaa Allahu zuwa yamma zai samu lafiya don Allah ta kula dashi ta amsa tare da godiya ta sauƙe wayan, ficewa tayi zuwa kitchen ta ga abinda suka fara a lokacin gari ma ya fara haske taje ta watsa ruwa don duk yadda ta motsa kamshinshi kaman tayi wanka da turarenshi kamshin na sakata jin kaman har lokacin yana kwance ne a jikinta rungume da ita Dukda ba don soyayya ko wani romance suka yi ba taimako ne ta mishi amma hakan ya mugun tsaya mata,bayan ta fito ta shirya cikin atampharta riga da siket da ya zauna mata chass ta ɗaura dankwali sai ta nemi gyale mai girma da kauri ta yafa ta fita parlor tana shirin shiga side dinshi aka yi mata sallama. "Mery ya dai?" "Wai wani likita ne ya zo duba Oga Rayyan" "oaky ki ce ya shigo" Tana nan tsaye har ya shigo suka gaisa kan ta mishi jagora har ciki, har lokacin yana kwance ba bacci kuma yake ba don zafin zazzabin bai barshi ba, tana daga chan gefe har likitan ya haɗa drip ya mishi allura ciki ya saka mishi canular yayi wani a canular kan ya ɗaura ruwan sai ɓata fuska take kaman ita ake ɓula wa. "Toh madam za ki iya samun ruwa masu ɗan dumi kaɗan da towel ƙarami a shafa mishi a kan nan da Goshi zafin jikin zai ragu Dukda na mishi allurai amma hakan ma na da kyau don temperature ɗin shi is very very high" "in shaa Allahu mun gode kwarai Dr" "Mention not" Daga haka ya fice, bayi ta tafi ta haɗa ruwan ta samo ƙaramin towel ta dawo bakin gadon ta zauna ganganshi ta cire gyalen ta ajiye tare da matsa ruwan ta ɗora mishi a Goshi ya buɗe ido ya kalleta saboda sanyin da ya ratsa shi yana sauƙe ajiyar zuciya mai nauyi, wani iri take ji da kallon nashi amma ta dake ta cigaba da shafa mishi da kanshi ya gaji ya mayar da idanun ya rufe sai ta sauke numfashin da ta riƙe tuntuni, idan ta zo daidai kwantaccen sajenshi sai ta tsinci kanta da zame towel ta bar fatar hannunta na shafa lallausan gashin wurin a hankali. Jin abin nata na so ya fi karfinshi ya ɗaga hannu ya ture hannunta, ta ɗan tura baki ta miƙe ta nufi bayi tana mita 'Mutum bama shi da lafiya amma hali ba zai chanza ba!' Sarai ya ji ta a maimakon ya ji haushi Sai ɗan murmushi da yayi a cikin zuciyarshi wanda ko alama bai fito fili ba, bata ma fito ba bacci ya ɗauke shi don akwai allurar bacci ciki daga nan ta ɗauki gyalenta ta yafa ta nufi cikin gidan, ɗakin su Abeeha ta shiga inda ta samu suna zaune sun yiyyi wanka Mommy da mama da suna nan tun rasuwar basu tafi ba suma suna ɗakin da alamu sun zo duba kwanansu ne. Har ƙasa ta duƙa ta gaishe su suka amsa cikin kulawa kan ta dubi jannah ta gaisheta tare da mata sannu da jiki suka gaisa da Abeeha a karshe, wata cousin ɗinsu Aaliyah ce tace "Na ga likita yana shiga wurin ku da safen nan Allah dai ya sa ba wani abu bane?" Kanta ƙasa tace "Wlh Ya Saraki ne ya kwana da zazzabi amma Alhamdulillah an saka mishi drip yanzu haka bacci yake" Cike da jimami suke mishi Allah ya kara sauƙi ta ɗan jima anan har aka gama fito da kayan kari ta karya anan suna hira kaman dama chan ita ma she's part of the family don basu ware ta ba sam. Sashensu ta koma ta leƙa ta samu har lokacin bacci yake ta koma parlor tana kallon time, a chan kuwa fitan ta ba jimawa sai ga su mommy sun shigo babban parlor aka dawo da gaisuwar makota dai kan shigo a yi gaisuwa da su Ƙawayen su Afeefah har ma da dangin mijin jannah ita dai Samha sai baza ido take ta ga ta inda Afeefah za ta ɓullo amma bata ganta ba. Ko da Saleem ya shigo suka gaisa Abeeha ya tambaya Rayyan fa don ya ta kiran wayanshi ba'a picking nan ta faɗa mishi ai bashi da lafiya an ma saka mishi drip kila bai tashi ba har lokacin, bai shiga ba don ya san akwai bambancin da da yanzu ba zai yiwu ya je har ɗakin ba sai fita yayi akan yana parlorn waje. Sai karfe sha ɗaya da rabi da Afeefah ta leƙa ta samu baya kan gadon alamar ya shiga wanka, gadon ta gyara tsaf kaman ba'a kwanta ba ta fice chan sai gata rike da tray mai dauke da dafaffen dankali sai wani curry chicken soup da ta mishi da kifi gasashe a gefe sanin yana so sai tea da ta haɗa mishi, ya gama shiryawa cikin riga da wando masu taushi don ba jeans bane wandon cotton ne mai ɗan faɗi Brown, shirt ɗin burnt orange ya karɓe shi sossai ya sake zama pale kana kallonshi zaka san yana ciwo. A kan table na gaban couches na ɗakin ta ajiye ta kalleshi shima ita ya kalla sai suka haɗa idanu ta ɗan rausayar da nata tace "Ina kwana Ya Saraki? Ya jikin?" Bata zaci zai wani amsa ba sai kuma taji ya ce "Alhamdulillah da sauƙi" Dukda a hankali yayi magana amma ta ji ta ɗan murmusa "ka karya sai ka sha magani" Ya nufo inda take sai da ya ɗan wuce taji ya ce "Thank you!" Zama yayi ya ja abincin ya shiga ci hakan ya faranta ranta sossai ta juya ta fice, a parlor ta zauna tana kallo kusan mintuna talatin sai gashi ya fito ya fita waje. Sai lokacin hankalinta ya kwanta ta miƙe itama ta nufi wurin su Jannah tana shiga babban parlorn da sallama suka hada idanu da Mommy... 🖤Gureenjoh🖤 HAIHUWA DA HANJI (A True life story) Fatima Muhammad Gurin (Gureenjoh) Wattpad-Gureenjo6763 Arewabooks-Gureenjoh ADABI WRITERS ASSOCIATION *FREE BOOK* *41* "Sannunku" Ta faɗa tana ɗauke kanta daga cikin idanun mommyn da ta kusa daskarewa a wurin a zaune. Bata ƙara firgita ba sai da taji matar uncle sanusi na cewa "Sannu Afeefah, jigilar nan ba zai haifar miki da ciwon jiki ba? Kece nan ke ce chan ya kamata kina hutawa fa" Matar uncle Mansur tace "Gaskiya kam ya kamata ki dinga ji da mijinki kawai su jannah duk ba ga mu nan ba, shima ba don baudadden halinshi ba ai da duk sai mu kula da ku don kema na tabbatar raunin tafiyar Mammi na nan ɗanye a zuciyarki." Murmushi ta ɗan saki tana zama za tayi magana Sameera ta miƙe tsaye don tun dazu duk su huɗun kaman an kafa su ne idanunsu ƙurrr a kanta. Nuna ta take hannunta na rawa "Afee...fah?" "Ita ce ko Ya Sameera? Ita ce ba gizo na gani jiya ba ashe!" Samha tayi saurin faɗa kaman jira take wani ya fara magana cikinsu. Mommy ta kasa ma magana tsabar yadda taji da ganin Afeefar ƙare mata kallo take yadda ta wani sauya tayi mugun kyau ko atamphar jikinta ka gani ka san bata cikin wahala sai hawaye suka fara zuba mata ta tuna ranar auren Saleem inda take ce mishi a lokacin Afeefah na chan tana raba wa maza kanta tana samun na cin abinci idan zai mantata gyara ya mantata. "Kun santa ne?" Mama tayi tambayar da mamakin irin shock da ta gani a tare da su ga mommy ta fashe da kuka. Jannah ce da daman ta kasa sakewa dasu saboda har lokacin bakinsu take gani akan abinda suka yi wa Afeefah tace "Sun santa Mama, mommy kin ga ta sauya ko? Kun ga yadda Allah ke ikonshi ko? Ku kun ƙi ta mu mun so ta mun karɓeta hannu bibbiyu, kun muzguna mata hakan bai hana ta muku taimako mafi girma ba a rayuwarku... Ita ce ta taimaka da ayoyi da ruwan tofi ba ji ba gani har saida ta tabbatar asirin da aka yiwa Ya Saleem ya karye, gata nan yanzu haka ana dawowa makaranta exams na karshe zasu rubuta tana kan karatu. Nasara mafi girma da daraja shine tayi aure ta auri namijin nunawa sa'a wanda ko cikin maza sai an tara dubu a samu tamkarsa ɗaya. Afeefar da kuka sani ce dai ita ce matar Ya Rayyan ta sunna a yanzu haka" Afeefah ta mayar da kanta ƙasa hawaye na taruwa a idanunta sam bata san sun zo gangarta ba sai jin mommy tayi ta riƙe hannunta tana sake ƙara fashewa da kuka mai tsuma rai, Abeeha ma bata yi shiru ba ta kara da labarin irin yadda ta taimakesu akan Saleem. "Don Allah ki yafe mana Afeefah, haƙiƙa ba mu da bakin neman yafiyarki saboda mun aikata miki ba daidai ba, mun kasa duba kasantuwarki mace mun kasa yarda cewa Allah ke komai a sadda ya so na bi dare na raba ki da Saleem karfi da yafi na aura mishi wacce nake ganin ta fi cancanta ashe ban sani ba ƙabari na haƙa mana... Haƙiƙa na so na ganki ba tare da aure ba nayi adu'ar Allah ya bayyana mini ke ko ta wani hali in nemi yafiyarki in kuma gyara kuskurena ashe ke kam Allah ya dubeki ya Musanya miki da alkhairinki... Don Allah ki yafe mana ki yafe mana Afeefah!" Sossai duk suke kuka suna neman yafiyarta sai ta nemi rudewa Dukda tayi mamaki amma ta sani duniya aka ce makaranta. "Mommy ku daina neman yafiyata wlh tun kafin na bar gidan duk na yafe muku Yaya Saleem ya wuce yadda kuke zato a wuri na. Ban riƙe ku a zuciyata ba ku daina wannan kukan don Allah". Samha ta fi kowa bata haƙuri sai Mommy, duk ta nuna ita komai ya wuce a wurinta suka koma gefe suna ta kallonta ko motsi tayi burgesu take, basu taɓa sanin haka take ba sai a yanzu yinin da suka yi a ranar suka kara sanin wacece ita kunyar duniya duk ya rufesu na tunanin duk irin wulakancin da suka yi mata, lallai da gaske ne da aka ce mai haƙuri shi yake dafa dutse har ma ya sha romonta. Mommy ta tabbatar Saleem bai san da wannan labarin ba, gab za su tafi ta kira shi a waya akan ya zo ciki duk jama'ar sun watse a babban parlorn sai Afeefah dake zaune tana duba abu a waya mommyn ta fito daga ɗaki ganinta yasa tace "Yauwa ashe kina nan dama ke zan je dubawa kitchen. Yanzu Saleem zai shigo ku gaisa..." Gabanta ne ya faɗi rabon da su hadu kusan watanni bakwai zuwa takwas kenan, ya rabu da ita cikin kuna da zafin zuciya tare da hawaye a yanzu zai haɗu da ita matsayin matar aure, matar ma ta abokinshi me zata ce mishi? Ta san akwai laifin mahaifiyarshi a rabuwarsu amma ta san dole zai ji zafin samun wannan labari, anya ma zai yi farin ciki da ganinta? Bata gama tunanin ba ta ji sallamarshi gabanta ya sake faɗuwa ta miƙe tsaye sai suka haɗa idanu a lokacin da take amsawa da iyaka lips ɗinta. "A...Afeefah? Ke..ke ce nake gani? Afeefah ba gizo idanuna suke min ba kece tsaye a gabana? Ta yaya kika zo gidan nan? Ina kika shiga Afeefah? Ina kika shiga...?" A ruɗe yake maganan idanunshi na cika da kwallah kaman yadda nata ya cika fal da hawayen ganinshi. "Ya Saleem...!" Ta faɗa a sanyaye sai ta kama hawaye. Sake matsowa yayi kaman zai taɓa ta tayi saurin matsawa baya sossai tana girgiza mishi kai. "Ka gafarceni Ya Saleem yanzu da baya ba ɗaya bane..." "Afeefah na san akan mahaifiyata ne wlh yanzu duk sun yi nadamar abin da suka aikata miki, na tabbatar za kuma su nemi yafiyarki don Kullum adu'arsu shine mu ganki mu nemi yafiyarki...ko babu komai a yanzu za mu cika burinmu za mu cika alkawarinmu na mallakar juna..." Daidai lokacin Rayyan ya sanyo kai parlorn he just stood there fuskarshi kadaran-hadaran yana kallonsu. Hawaye take yi sossai "Lokaci ya riga ya ƙure ya Saleem, kayi hakuri Allah bai nufa na zama rabonka ba. Ni din yanzu matar aure ce." Jikinshi yayi wani irin sanyi wani tashin hankali da damuwa na lallaɓo wa ya rufe shi murya na shaking yake furta "A..a..aure Afeefah? Aure kika yi? Da waye? Me..me yasa?" Idanunta ne suka shiga cikin na Rayyan da sauri ta kawar heartbreat ɗinta na kara gudu ganin kallon da yake mata. "Ka sa a ranka ƙaddara ce ta zo haka, amma ni matar aure ce don Allah ka ajiye zancen alaƙar da ta riga ta wuce Ya Saleem" Daga haka tayi saurin wucewa sashensu ta barshi kanshi a matukar kulle, idan bai ce ya matuƙar kaɗuwa da wannan zance ba yayi ƙarya zuciyarshi raɗaɗi ya shiga mishi, saboda rauninshi tuni hawaye suka shiga zubo mishi haƙiƙa ya so Afeefah kaman ranshi har gobe yana ƙaunarta amma gashi ƙaddarar su ya zaɓar musu rabuwa aure tayi a sadda yana chan ya rasa hankalinshi, me yasa bata yi haƙuri ba? Meyasa bata jira ba? Me yasa yayi jinkiri? Tun da ya dawo hayyacinshi a neman ta yake ko Allah zai sa ya ganta ashe ita kam tana chan tare da mijinta tana rayuwa mai kyau don ko skin ɗinta ya bayyana hakan. Mommy ce ta fito ganin yanayin da yake ciki ta kalli Rayyan dake tsaye har lokacin a bakin kofa hannunshi harde a kirjinshi wanda da alama Saleem ɗin bai kula da wanzuwar shi ba tayi saurin kama Saleem ɗin ta zaunar taje ta kawo mishi ruwa bai karɓa ba sai ma maganganu da ya fara "Mommy ta ya kika ga Afeefah? Me ya kawo ta gidan nan? Mommy wai da gaske Afeefah aure tayi? Aure tayi? A yanzu haka Afeefah ta haramta mini?" Mommy ta kalli Rayyan ta mayar da idanunta kan Saleem. "Saleem Afeefah ta yi aure laifina ne duka, laifina ne ta subuce maka ka yafemin ciwon da nake sakawa zuciyarka ka ɗauki dangana da haƙuri. A gidan nan muka samu Afeefah tana kuma auren abokinka ne Rayyan..." Da ƙarfin gaske ya miƙe har yana Buge ruwan hannunta ya faɗi ƙasa "Rayyan?? Mommy all this while Rayyan na tare da Afeefah? Har ma ya aureta? Rayyan dai Rayyan Moh'd Khamis??" Gabaɗaya wani duhu ne ya taso ya rufe mishi gani tsabar wani irin bacin rai da ya zo mishi juyawa yayi zai fita yaje ya samu Rayyan ɗin sai suka haɗa idanu nan ya nufe shi ya tsaya a gabanshi. "Rayyan da gaske Afeefah ka aura?" Shi karan kanshi ya san yayi mugun ƙoƙari a sadda ya buɗi baki ya furta "Saleem Afeefah matata ce idan har ka san darajar aure da kuma martabarsa za ka kiyaye irin kalmanka a kan matata... Ƙaddara ta riga ta raba ku ta bani ita a lokacin da ban yi zato ko tsammani ba don haka don't Look at me with those eyes dake nuna kaman I betrayed you or something like that, you should questioned yourself nd your family not me..." Yana kai nan ya wuce don har ga Allah bai san dalilin da yasa yake ji kaman zai kama da wuta ba, mommy ya kalla har kaman zai wuce ya tsayar da idanunshi kanta ba zai iya yi mata magana kai tsaye ba ba kuma don komai ba sai don uwa ce ya juyo ya kalli Saleem dake kallonshi rai a tsananin ɓace yace in a respectful manner. "Rasuwa aka yi mana ko ba rasuwa ba muna da darajar da ba za'a tako har nan a ci mana mutunci ba Saleem, idan ba zaka taya mu baƙin ciki da jajen rasa wani sashe na bangonmu ba za ka iya zama da kai da familyn ka a gida. Mun gode" Daga haka ya nufi sashensu ya bar su nan tsaye calmly kaman ranshi ba suya yake ba. Wani irin duka Saleem ya kaiwa bangon wurin yana yin baya tare da zuba yatsun shi cikin gashin kanshi kaman zai fashe haka yake ji, su Samha ne duk suka fito a tare da Abeeha jin salatin mommy. Ganin yanayin da suke ciki suka shiga tambayar me ya faru? Menene? Mommy tana zubar da hawaye tace "Na sake wani kuskuren, da na san hakan zai kasance Saleem da ban nemi ku gaisa da Afeefah ba! Na zaci zaka yi farin cikin ganinta idan ka ji kuma tana da aure zaka taya ta murna da Adu'a ka karɓi kaddara amma me kayin nan? Abokinka ne fa Rayyan abokin da ya zama ɗan uwa ya kuma tsaya mana duka a sadda muke neman tagayyara. Rasuwa fa mahaifiyarshi tayi ko lafiya bai samu ba me kake yin nan?" "Rayyan ya ci amanata mommy, ashe ya san inda Afeefah take ya zaɓi ya ɓoye min? Ashe aurenta yake shirin yi ko da na matsa ya nemo min ita a sadda ba ni da daman hakan saboda kalamanki ya san inda take ya dinga zurma ni akan ya neme ta ya rasa? Meyasa tun farko bai ce min sonta yake in sakawa zuciyata hakan ba? Idan ba da wata manufa yayi hakan ba Meyasa ina zuwa gidan nan bai taɓa nuna min tana nan ko ya bari na ganta ba?" Abeeha da ranta yayi mugun ɓaci tace "Ya Saleem baka kyauta ba sam...! Ban zaci ko Ya Rayyan amanarka ya ci zaka iya aikata hakan kuma ka jefe shi da irin kalaman nan ba. kar hankalinka ya gushe mana... Toh wallahi Yaya Rayyan ya auri Afeefah ne bisa umurnin Mammi, ya karɓi auren cike da tunanin mai zaka ɗauki hakan a duk sadda ka dawo hayyacinka... Idan ma ya faɗa maka a lokacin kake nemanta cewa coincidently sun haɗu a sadda ta taimaki Mammi Mammi ma ta taimaka mata ta kawo ta gidan nan me zaka yi? Kar ka manta a sannan Allah ya isan mahaifiyarka ke kanka muddin ka mata magana? Idan da yana da mugun nufi kanka da ba zai ba da gudummawar dinga kawo ka gidan nan kana ci da sha daga ayoyin Allah ba har ka dawo cikin hayyacinka...idan da yana da wata manufa ta daban da ba zai bari ku kasance tare da ita a zaman makonkin nan ba don kaima ka san zai iya kaita ko ma inane... Wallahi ko ni bayan labarin da Afeefah ta bamu na ji har abada ban bata goyon bayan aurenka ba, Mammi ta zaɓa mata miji kuma ta karɓa hannu bibbiyu kuma take ibadar aure... Ko da Yaya Rayyan baya sonta a baya bai kyamaceta ba Dukda ya san labarinta kaman yadda kaima baka kyamaceta ba bambancin kawai mu da mahsifiyarmu muna sonta kuma muna so rayuwarta ta inganta ashe idan baka godewa Ya Rayyan ba ba zaka ga baƙin shi ba. Ka je kayi nazarin kalamaina kan ka sake yanke kowani irin hukunci ne" Tana kai nan ta juya ta koma ciki cike da jin haushinsu dukkansu, tunanin ta ya tsaya akan ya Rayyan da banzar zuciyarshi Allah ya sa kar ya sauke akan Afeefar. Tana zaune bakin gado ta toshe bakinta da gyalen ta tana kuka kawai taji an turo kofan an shigo, da sauri ta ɗaga idanunta dake zub da hawaye sai suka shige cikin nashi da ya jirkice, wani irin kallo ya mata da ya sa tayi saurin mayar da idanunta ƙasa tana Miƙewa tsaye. "Kin raina ni ko? Ni za ki wulaƙanta??" A hankali yayi maganan. Sai ta ɗago tana cewa "Kayi haƙuri ban san zai shigo ba, ban san mahaifiyarshi ta kira shi ba da na nemi izini..." "Shuttt up!! Just shut up Afeefahh" Ya daka mata tsawa har saida ta tsorata tayi baya baya zata faɗi ta dafe jikin gado kirjinta na sama da ƙasa. Yau ne karo na farko da taji sunanta a bakinshi Dukda kaɗuwar da tayi hakan bai hana sunan sake amsa kuwwa cikin kunnuwanta ba da muryarshi. Shiru yayi yana sauke numfashi idanunshi a tsaye a kanta ya ce a zafafe "Ko babyn roba na aura, ko 'yar tsana ce ta amsa sunan matar Rayyan Moh'd Khamis wallahi billahi na fi ƙarfin ta wulaƙanta min aure... A gabana kike cewa aurena dake ƙaddara ce??" "Ka yi ha..kuri ba haka..." Juyawa kawai yayi ya fice yana buga kofar da karfin gaske sai da ta sake razana. "Na shiga uku!" Ta ambata tana zama bakin gadon. 🖤Gureenjoh🖤 HAIHUWA DA HANJI (A True life story) Fatima Muhammad Gurin (Gureenjoh) Wattpad-Gureenjo6763 Arewabooks-Gureenjoh ADABI WRITERS ASSOCIATION *FREE BOOK* *Yauwa. Ga Page ɗin ku na yau, it's monday already! ba ni da tabbacin zama available through out.* *42* Zaune kawai yake a kan couch bayanshi na jingine da jikin kujerar idanunshi a lumshe, tun da ya dawo daga Sallar isha haka yake. Wani iri yake ji lokaci lokaci ya kan buɗe idanu ya kalli kofan ko za ta shigo amma shiru babu ita ba alamunta, sai wuraren sha biyu ya miƙe ya ɗan yi shirye-shiryen shi na bacci ya koma gado ya kwanta sai ya tsinci kanshi da kallon wurin da take kwanciya a kwana biyun yadda inuwarta ke yi, irin rikicewar da tayi ta rungumeshi a daren jiya hannayenta na yawo a cikin sumanshi da bayan wuyanshi ya tabbatar da ana lafiya ne ba za ta taɓa iya hakan ba, sai yaji emptiness da ya rasa na menene, da kyar yayi bacci bayan ya yi overdosing magungunanshi. Ta ɓangaren ta tana so taje ɗakin amma tana tsoro, kila bai huce ba kar taje kuma ya hau ta da faɗa ko ya make ta, haka ta shirya ta kwanta a kan gadonta sai ta dinga tunanin moment ɗinsu na jiya sautin numfashinshi na dawo mata har heart ɗinta na racing a haka bacci ya ɗauketa. Karfe goma na safen Washegari ta fito a shirye cikin half boubou da skirt na lace cream colour da mix of dark pink yayi mata kyau sossai ta yafa pink gyale bayan dan kunne da wani zoben gwal dake yatsanta bata wani saka acessories ba ta fito zuwa babban kitchen ta karbi abincin su ta kai ta shirya a dining kan ta koma wurinsu jannah da Uncle ya kira mijinta ya zo ya dauƙeta yau duk su mama ma yau za su koma gidajensu. Shi kam tun da ya dawo Sallar asuba bacci bai ɗauke shi ba yana zaune kan kujera inda kaman nan ne wurin zamanshi a ɗakin, as usual idanunshi a rufe ruf bai motsa ba har sai da Abeeha ta kira shi a waya akan su Mama za su koma gidajensu ya miƙe ya fito suka sake mishi gaisuwa da ban haƙuri kan suka tafi bayan sun raka su har waje, ya kalleta amma bai tsawalla kallon ba don haushin ta har lokacin yake ji barin ma da ya kalli yadda idanunta suka zama saboda kukan da tayi jiya Dukda ba kowa zai lura ba amma shi with a single gaze ya fahimci lids ɗin are swelled up a little. Bai koma ciki ba motar Sulaiman ya shigo gidan sai suka isa kan kujerun da aka shirya don hutawa a chan gefen gidan suka zauna. "Ya dai? Na ga kaman ranka a ɓace sossai?" Sulaiman yayi tambayar don a hankali Sulaiman ɗin yayi mugun karantar shi har ma ya zama kaman Saleem a wurinshi ɗan zaman da suka yi daga aurenshi zuwa yanzu rasuwar Mammi. "Hakane am just worried sick about one or two things." Sulaiman ya gyara zama "Toh fa, menene kuma?" Nan ya bashi labarin duk abin da ya faru Sulaiman sai yayi murmushi "Are you jealous?" "Menene hakan?" Yayi tambayar kaman bai san me ake nufi da kishi ba. "Rayyan kana kishin Afeefah ne sossai kayi adu'ar sassaucin zafin kishi, anan dai zan baka laifi Saleem ko da bai auri Afeefah ba kaman Yaya yake a wurinta sannan Saleem yana da fahimta am very sure bai san reasons naka bane yasa ranshi ya ɓaci, shima fa mutum ne kaman kai yana da zuciya a kirji, your words are harsh gaskiya kenan.." Ya gyaɗa kai "I know, tun jiyan i wanted to call him amma sai na bari ya huce tukuna. I just lost control tunda ta furta wai aurena kaddara ne kalaman sun min zafi" Dariya Sulaiman ya fara "Kana wasa da So Surgeon General Ryan Khamis, kuma fa babu wani abin zafi a maganan nan kishi ne kawai irin naka... Ai komai ma mukaddari ne daga Allah ta wani mawaki yace Nufin Allah ne! Haɗin Allah ne ko da basa so su gani sai anyi! Ka ga kenan dole da kaddara a komai. I'am advicing kaje ka samu Saleem ku yi resolving issue ɗin nan" "Kai! ka fa dameni da zancen kishin nan idan ma kishin ne ai ban yi laifi ba a gaban ka na cire kuɗina na biya sadaki!" Yayi maganan da iyakan gaskiyarshi yana sake kame fuska Sulaiman yana ta dariya. Basu jima ba ya wuce, shima ya shiga ya zari key bai ko bi ta kan abin kari ba ya fice daga gidan kai tsaye gidan su Saleem ɗin ya tafi, bai shiga ciki ba ya kirashi a waya akan yana waje mintuna kaɗan sai ga Saleem ɗin ya zo ya buɗe kofan motar ya shiga ya zauna ba tare da ya ce komai ba. "Ka tashi lafiya?" Rayyan ɗin ya faɗa, bai jira amsar Saleem ba ya ɗora da. "Na zo ne in baka haƙuri akan abin da ya faru tsakaninmu we are not perfect in everything sannan a zaman tare dole watarana a saɓa. A koyaushe kai ke haƙuri da ni I really respect and appreciate you Saleem kuma ka fi karfin duk abinda kake zato a gareni! Saleem...Billahi ban ɓoye maka wanzuwar Afeefah a gidanmu saboda son zuciya ko wata soyayya ba don har yanzu ban sani ba shin ina sonta ko ba na sonta na dai san ban tsane ta ba" Ya ɗan yi shiru kadan kan ya cigaba "A lokacin da muke waya da kai akan Mommy ta kore ta na ganta amma ban zaci saboda kora ne take tsaye a kan titi ba, jin irin damuwar da ka shiga ya sa nayi deciding in koma in ɗauko ta kafin ka samu masalaha da mahaifiyarka, ko da na koma ban sameta ba a sannan aka kira ni ba'a ga Mammi ba cikin damuwar rashin ganinta na tafi asibiti ka san halina farin sani damuwa na ba komai bane illa kar a samu wasu su cuceta ko su zalunce ta sanin bata san gari ba. ko da na isa asibitin sai na samu ashe ita ce ta taimaki Mammi, from there Mammi ta fara ƙaunarta har ta mayar da ita gida ba tare da na ce musu komai akan labarinta ba Dukda na san Mammi da su Abeeha amma ba zan so ta samu matsala a gidan yadda ta samu a naku ba, nayi tunanin faɗa maka sau ba adadi ina tsoron saka ka cikin wani damuwar don na san in har ka san inda take ba lallai ka cigaba da yiwa mahaifiyarka biyayya ba, zai iya zama ka saɓa umarnin ta saboda mace ko kuma shaidan ya ja ka ga fushintan ta hanyar yarinyar, na bari akan daga baya idan kayi settling komai sai na faɗa maka. Unfortunately abun nan ya zo ya faru tsakaninka da ex wife ɗin ka da i even called her name to your ears ka nuna baka santa ba kana da mata..." Daga nan ya bashi labarin duk yadda aka ɗaura aurensu da Afeefah. "Na karɓi auren ne saboda Mammi Dukda ta rokeni ya zama saboda Allah zan yi wa Afeefah komai ko da bata nan zata samu peace of mind na cewa ta barta inda ba zata wulaƙanta ba, na san Afeefah ce tayi adu'o'in duk da kake using na seven days a gidan mu ban damu ba saboda na san ka cancanci fiye da hakan daga gareta, ko da ka samu lafiya kafin mu yi maganan Allah ya kawo ajalin Mammi... Wallahi idan da za ta zaɓe ka Saleem ta tabbatar min za tayi farin ciki a tare da kai zan iya sakinta ka aureta... Saboda burin Mammi shine ta samu farin ciki da natsuwa a duk rayuwar da zata yi. I am terribly sorry da kalamaina na jiya i hope you forgive and forget ban san me ya hau kaina ba." Ya sauƙe numfashin wahala don ya gaji matuƙa da maganan, Saleem ya ɗauki ruwa dake tsakiyar su ya buɗe mishi ya miƙa mishi sai ya karɓa ya kurba kaɗan ya mayar mishi sai suka ɗan murmusa. "Kishi ne ya hau kanka ba komai ba" "Ana kishi haka siddan ne? Dazu Sulaiman ya gama ranting about that!" Saleem yayi dariya yace "Lallai kai sabon shiga ne, ai ba'a kishi babu So irin nakan nan ma mai zafi ne ƙanwata ta ma zuciyarnan dabaibayi ba zaka farga ba sai ka gama zurmawa saura mu saka ƙasa kawai mu binne" Murmushi mai sauti Ryan yayi bai ce komai ba. Saleem ya dube shi yana sauƙe numfashi "A haƙiƙanin gaskiya nima a sadda na dawo na kwana da tunanin actions ɗina na jiya, kawai na saka a raina cewa ban samu labarin bane ta yadda ya dace hakan ya haddasa saɓanin da muka samu. Tun a jiyan tun da na fita daga gidanku na riga da na sakawa raina har Abada Afeefah matsayin ta ɗaya da su Samha a gareni, ban san wani irin rabo bane ya haɗa ku ban san me Mammi ta hanga ba ta haɗa ku but i believe har karshen rayuwarku Afeefah ba zata yi kuka da kai ba muddin ta iya tafiyar da kai! Menene burina dama?" Ya ɗan ja numfashi "Burina ɗaya da Mammi shine ta samu rayuwa mai kyau and am very sure tunda ta karɓi auren take zaune lafiya she accept it with all her heart and soul to na me zan damu? Abeeha... She's so brave kalaman ta sun shigeni sossai da sossai am also sorry for what happened Ina yi muku Fatan alkhairi i also hope and prays za ka bani daman zama ɗan uwan da ba ta da shi a rayuwarta" Murmushi Ryan yayi ya ɗago ya kalleshi "Anya zan amince? ai sai ku haɗe min kai Thats the role that Sulaiman is playing fah" Saleem yayi dariya. Kallon gidan Ryan yayi "Why are you guys still here ba ku takura ba?" Saleem ya ɗan yi tsaki yana sake kallon gidan shima "Mun takura fa kawai rasuwar nan shi yayi delaying ɗina da yanzu mun koma Nan gidannan nawa na Malali already an gama komai maybe gobe we move out" Kai ya gyaɗa suka sake hira kaɗan a kan aiki kan suka sallami juna Rayyan ya fice Saleem ya koma ciki hankali kwance. Ya dauki hanyar unguwar su kenan aka kira shi a waya ya duba ya ga uncle Musa ne, dagawa yayi cikin ladabi suka gaisa "Ina so dama na ganka ne Ryan idan ka samu dama ko yanzu ka zo." "In shaa Allahu Baba gani nan zuwa" Juya motar yayi ya nufi Unguwar sarki inda nan ne gidan uncle musan yake. Yana zuwa ma ana kiran azahar yayi alwala suka shiga masallacin tare suka yi sallah kan suka dawo ciki, an kawo mishi abincin rana don haka a tare suka ci kan uncle Musa ya dube shi "Ryan ka san idan mamaci ya mutu ana so a yi gaggawar sauƙe mishi duk wani nauyi har gado, Toh zaman dai ya kamata mu yi da Abeeha da jannah ne amma sanin kana gaba da su kuma kai uba ne a gare su yasa na fara kiran ka, wannan takardu" Ya miƙa mishi ya karɓa yana dubawa Dukda komai na Mammi ya sani, haka komai na su Abeeha da jannah na wurin babansu dake hannunshi wanda Mammi ta sakar mishi yake kula musu da shi duk ya sani. "Mamanka ta ce in tabbatar maka ita ta baka halak malak har abada baya cikin abinda za'a raba nata" Da sauri ya kalli Uncle Musa. "Rabin dukiyar ta ne fa anan" "Eh, ta saka hannu zaka gani lawyer ɗinta ya saka akwai kuma shaidu akan hakan. Ta mallaka maka rabin abinda ta mallaka wanda gado ne daga wurin mahaifinta kyauta" Dukda arziki baya gabanshi kyautar ya kaɗa shi sai yana jin sabuwar Soyayya da kuma tsananin kewa na Mammin, idanunshi suka sauya sossai ya kalli uncle da ya sake cewa "Wannan kuma sauran rabin abinda ta mallaka ne na su jannah shima ta ce ne in bari a hannunka kai zaka zauna da su idan suna bukata ka basu idan sun bar maka ajiya ta tabbatar za ka juya musu yadda ya kamata" Karɓa yayi yana jin wani iri sossai da sossai. Da kyar ya haɗa natsuwar shi wuri guda yayi godiya wa uncle ɗin kan ya fice daga gidan ya nufo gida. Yana parking wayanshi ya ɗauki ringing ganin ogansu ne yasa yayi picking tare da saluting maganan mintuna biyar suka yi ya sauke wayan tare da bude media group dinsu, news dake yawo ya zubawa idanu sama da mintuna goma ba tare da ya sani ba kan yayi baya baya ya jingina da kujera wani irin abu na tsaya mishi a tsakiyar zuciya, sossai news din ya jijjigashi amma yana iya kokarinshi wurin ganin ya danne don in ka kula har jikinshi rawa yake sai lumshe ido yake yana buɗewa lip dinshi na ƙasa a ɗan datse tsakankanin hakwaranshi. Sai da ya gaji ya buɗe murfin motar ya fita ya nufi cikin gida, a babban parlor ya samu jannah da Abeeha suna zaune shima ya zauna suka gaishe shi ya amsa da kulawa ya dubi jannah "Yaushe kike shirin komawa ne kam?" "Dama yau ne to kuma ya tafi Abuja ɗazu yace in zauna kawai gobe zai dawo in ya dawo zai biyo ya daukeni sai mu wuce gida" Cikin girmamawa tayi magana. Ya gyaɗa kai Nan ya musu bayanin gadon su tare da fitar da papers ɗin ya ajiye. Abeeha tace "Ni dai Yaya bana bukatar rike komai a hannuna gaskiya, babu abinda ka rage mu dashi ko da Mammi ke raye baka barta ta mana komai da kuɗinta ba don haka ka haɗa duka ka riƙe a wurinka kawai." Jannah ma tace "Gaskiya nima dai babu abinda zan yi dashi a yanzu, kana min ko da nayi aure baka daina ba shima kuma bai rageni da komai ba for now ka bar wannan a hannunka yaya" Kai ya gyaɗa ya dubi Abeeha "Gobe zan tafi wani aiki chan Gabas maso yammacin ƙasar nan ban san adadin kwanakin da zan yi ba don haka ki duba ki rubutu duk abinda za ku bukata da safe zan kaiku shopping sai a saya" Godiya ta mishi da Adu'a. Ya miƙe ya nufi sashensu. Afeefah na zaune shiru cike da tunaninshi, bai karya ba hakan ya dameta sossai har take jin babu daaɗi sai tunani take ko ina ya je? Ko yana lafiya? Tsoronta ma ya sha magani? Kar zazzabi ya dawo mishi yana ta yawo a rana duk ita kaɗai dai ta yanke dole zata bashi hakuri ta kuma fahimtar da shi ba da wani manufa ta aikata abinda ta aikata ba. Ta miƙe zata fita wurin su Abeeha kenan shi kuma ya shigo, kallo ɗaya ya mata ya ɗan ɗauke kai sai yayi sallama yadda zata ji ta amsa tare da cewa "Sannu da dawowa Ya Saraki" Ya ɗan lumshe ido ya buɗe kan ya ce "Yauwa" Daga haka ya wuceta ya nufi ɗakin shi bai bata daman magana ba kenan har yanzu fushi yake, jiki a sanyaye ta fice wurin su Abeehar anan take jin labarin wai zai tafi wani Assignment gobe ba lallai ya dawo kusa ba jikinta ya sake yin sanyi ƙwarai har bayan Magrib bata san me zata yi ba, luckily ko da ta ajiye mishi abincin dare ya ci. Bayan tayi isha ta gama shiryawa cikin cotton Light blue riga da wando dogo na kayan bacci ta ɗora navy blue hijabinta har ƙasa ta nufi ɗakinshi don ta yanke zuwa kawai ta bashi hakuri kar ya tafi yana fushi da ita. 🖤Gureenjoh🖤 HAIHUWA DA HANJI (A True life story) Fatima Muhammad Gurin (Gureenjoh) Wattpad-Gureenjo6763 Arewabooks-Gureenjoh ADABI WRITERS ASSOCIATION *FREE BOOK* *Tsakani da Allah ba ni da abin da zan ce da masoya sai na gode, ina ganin irin ƙaunar ku gareni. Na gode kwarai da gwalagwalan adu'o'inku. Ta Baba Makkah kin faranta min kwarai, sai masoyinka na haƙiƙa ne zai tuna da kai a gaban ɗakin Allah har yayi maka Adu'a da Fatan alkhairi don haka wannan Page ɗin sadaukarwa ce gareki Allah ya bar zumunci har a aljannah, Allah duk ya dube mu ya biya mana buƙatunmu na alkhairi.* *43* Ta ɗan jima tsaye jikin ƙofan tana tunanin ta shiga ne ko kar ta shiga? Da kyar ta tattaro kuzarinta ta ɗan yi knocking kan ta tura kofar ta shiga gabanta na tsananta faɗuwa. Hasken ɗakin ba shi da wani yawa don haka tsaf take kallonshi zaune tsakiyar gado jingine da pillow gabanshi system ne yana kallo, idanu ya ɗan zuba mata tana tahowa a hankali har ta isa jikin gadon ta ɗayan side ɗin inda shi kuma yana jingine ne da side ɗin da ya saba kwanciya. Muryarta na fita a hankali cikin tsoron faɗan shi ta shiga furta "Na na..zo ne mu yi sallama na ji wai za kayi tafiya, kuma ina so ne in baka haƙuri wlh ban san kalmar ba zata yi maka daaɗi ba. Don Allah kayi haƙuri." Tun da ta shigo ya ɗauke kanshi daga kan system ɗin ya zuba mata ido sauƙar muryarta a kunnuwanshi ya sa Ya ɗan lumshe idanun ya sake buɗewa a kanta. chan ƙasan muryarshi yace "Zo nan." Bai cigaba da kallonta ba sai ya mayar da idanunshi kan system dake aiki gabanshi wanda kallo yake na wani horror movie, tun da yayi shirin kwanciya tunaninta ya so ya dameshi sam shi bai ma san me yake damunshi ba daga dan kusancin da suka samu kwana biyu shikenan kuma sai a ta shiga lokacin hutawarshi ta hana shi hutawa da tunaninta? System ya jawo ya fara kallon dole sai kuma Allah ya jefo ta. A hankali ta hau gadon kamshinta na dukan shi har yana jin bugun zuciyarshi na sauya wa. Idanunshi ya kai ga kallonta ganin tana chan nesa ya ce "Matso nan" Ya taɓa gefenshi, a ɗan tsorace cikin bugun zuciya ta matsa tana dana sanin zuwanta ɗakin don ji take kaman zuciyarta za ta fito daga madaukarta don tsabar bugu, inda hannunshi yake ta matsa kaman an ce ta kalli fuskan computern aka nuno wani abin tsoro da ya firgigita don ta tsani film mai abin tsoro za ta gudu ya riƙo tsintsiyar hannunta babu zato sai gata bisa kirjinshi daga gefen kafadanshi ya mayar da hannunshi na wurin ta bayanta inda tayi saurin binne kanta a kirjin nashi sihirtaccen kamshin shi na sake shiganta yana ƙara bugun zuciyarta, baya baya yayi ya jingina da gadon yana sake kara kusantar da ita jikinshi. Bai ce komai ba ya cigaba da kallon yayinda tayi shiru kawai tana sauraran bugun zuciyarshi, sun kwashe sama da awa guda a haka ko da ya gama ya ɗan ɗago ta zai yi magana kawai ya ga tayi bacci, ya san kwanakin tana ƙoƙari kuma bata samun isashen bacci yadda baya yi itama bata yi, gwara ma shi da safe ya kan taɓa amma ita ko da safen baya ganin tana yi sai zirga zirga. Hijabin ya zare mata ya jefar ya zubawa fuskarta idanu yana kallo, bai san me ya riƙe shi a fuskar ba ya dai tabbatarwa kanshi da she's Drop-dead gorgous wanda bai taɓa fahimtar fuskar ba irin yau, kallon natsuwa yake binta dashi da ya rasa dalili a hankali ya furta "what's wrong with me?" Ya kai hannunshi ɗaya yana jin zuciyarshi na pounding har sound ɗin na iya shiga kunnuwanshi... Yana so ya kwantar da ita akan pillow amma sai ya ji ba zai iya ba don haka ya gyara kwanciyarshi ya gyara mata ta yadda rabin jikinta na a nashi ya lumshe idanu ga mamakinshi tunaninta ya cigaba da yi Dukda gata jikinshi da kyar bacci ya ɗauke shi. Basu farka ba har aka shiga masallaci suratul Fatiha da ake karantawa shi ya farkar dasu duk su biyu lokaci ɗaya ta yi saurin Miƙewa zaune tana ɗan matsawa kanta ƙasa, ya ɗan kalleta kadan yadda tayi kaman wacce aka kama tana sata ya sa ya ɗan yi murmushin da bai fito ba ya sauka ya shige toilet, hijabinta ta ɗauka ta sauƙa ta gudu. A bayi ta tsaya tana kallon kanta, bacci fa ta sake yi a jikinshi comfortably? Wayyoo Allah ta ayyana a ranta tana dafa zuciyarta, gashinta da tayi parking cikin messy burn ribbon ɗin ya fice bata ma san ta baro a ɗakin ba, da kyar ta haɗa tunaninta wuri guda tayi alwala tazo tayi sallah ta kwanta a wurin, sai Eight ta fito a shirye cikin Abaya Grey da yayi mata kyau sossai hula ne a kanta kai tsaye taje ta dubo abincin taga wanda zai iya ci ne ta kwaso ta kawo sashen nasu ta shirya dining ta saka turaren wuta a parlorn don a gyare yake tsaff yana kyalli ta juya zata koma ya buɗe kofa ya fito, kallonshi tayi yana sanye da wani Army Green riga tare Black wando da ya amshe shi, rigan ya kama shi ya fitar da kirarshi sossai bai mishi ruwa ba sam sai taji wani nauyin shi ya rufeta ta mayar da kanta ƙasa, ya kalleta ya ɗan shafa gashin kanshi kaman zai yi magana kuma sai ya nufi dining kawai. Binshi tayi sai da ya zauna tace "Ina kwana?" "Kin tashi lafiya?" Ya bata amsa ko numfashi bai bari ta ƙarasa saukewa ba idanunshi na akan fuskarta sai kawar da ido take daga kallonshi wanda hakan ma dariya ya bashi amma ko a fuska bai nuna alamu ba, ta haɗa mishi abin kari da yau English breakfast suka yi a gidan ta tura mishi, bata so ta tafi tayi laifi don haka ta ɗauki omlet ɗaya ta haɗa tea ta ja kujerar da take zama chan nesa dashi ta zauna tana karyawa, bai ce mata komai ba itama bata ce ba. Bayan ya gama ya miƙe ya koma ɗaki ta bishi da kallo tana ɗan taɓe baki mutum kaman hawainiya, tattare wurin tayi tsaf kaman ba'a ci abinci yanzu ba ta wuce nata ɗakin, monday za ta fara waec don haka dole ta fara duba takarda kafin taje ta faɗi sai ta fara lalabo takardunsu na makaranta ta ɗauko wayanta ta fara bincike akan past questions da take son fara dubawa. Shi kam kusan sai da ya gama haɗa duk abin da zai buƙata lokaci lokaci yana dan daakatawa ya tafi nazari kaman wanda baya kaunar tafiyar kan ya ɗauki keyn mota da wallet ɗin shi ya fito sanye da wata White sneakers da ta sake fito da shigar tashi idanunshi ya rufe da baƙar space sai ya zama kaman wani model ya san kan wanka ba laifi, a babban parlor ya samu su Abeeha suna ganinshi kuwa suka miƙe tsaye don dama sun shirya saboda sun sanshi yadda ya washi jira sai dai a jira shi... Har sun nufi kofa yace "Ina take?" Duk tsayuwa suka yi Abeeha na so ta tambayi ita wa amma fuskar shi da ba'a sake ba yasa tace "Afeefah ina ga bata san da ita za'a yi fitan ba bari na ƙirata" Ta ƙarasa tana nufan sashensu a ranta tana adu'ar Allah ya sa ita yake nufi kafin ya fara mata masifa, sai taga ya fice daga parlorn jannah ta bi bayanshi. Zaune ta sameta hankalinta kwance "Tashi maza ɗauki gyalen ki muje" "Ina za mu?" "Shopping Ya Rayyan ya riga ya fita yi sauri kafin ya hasala" "amma ni ba abinda nake bukata fa Adda Abee..." "Ke wlh tunda ya neme ki sai kin je, gwara kin tashi" Bata fuska tayi don wlh bata son zuwa ko ina, kai Abeeha ta gyaɗa "Ki same mu a mota kuma ki yi sauri" Miƙewa tayi ta chanza Abayar jikinta zuwa wani orange, ta saka farin takalmi tayi wrapping kanta da farin Jersey veil ta ɗauki wayanta ta nufi waje har lokacin fuskarta ba'a sake ba. Tun da ta fito ya zuba mata idanu ta cikin glassses na idanunshi yana kallo, a fuskarta ya tsayar da idanu yadda take dan ɓata ran ya bi jikinta da kallo Dukda ko ina a rufe yake sai da ya ɗan ji wani iri, tafiyar ta kaman tana rausaya Dukda ita sauri take, bai ji haushi ba idan ma zai yi judging wani gefen na zuciyar tashi akan gaskiya zai ce he enjoyed the walking ba tare da ya san dalili ba, tuni su Abeeha suna baya dole ta buɗe gaba ta shiga ya ɗan lumshe idanu saboda kamshinta da ya shige shi ya buɗe tare da tada motar ya fice daga gidan. Su Abeeha sun zaci ba zasu wuce shopping malls da suka saba zuwa ba na nan kusa kusa ko market square ko barnawa shopping complex sai suka ga ya miƙa ma yayi chan unguwar rimi bai tsaya ko ina ba sai Kaduna Galaxy Mall yayi parking suka sauƙa tana shirin sauƙa yace "Ki ji!" Ta ɗan kalleshi tana dawowa ta zauna "Na'am Ya Saraki?" Ya zare glass ɗin ya kalleta sai ta kawar da kanta, kaman zai mata gargadi akan wannan sarakin da take faɗa take motsa mishi zuciya sai ya fasa. "Kina ɓata rai babu abin da kike buƙata ne?" Ta Yi mamakin yadda ya karance ta Dukda tunda suka fito babu wanda yayi magana a cikinsu. "Kin min shiru ina magana?" Ya faɗa ba da faɗa ba... "A'a akwai, za mu fara waec monday akwai abubuwan da nake buƙata na makaranta sai da na fito na tuna" Bayan ta gama bayanin kuma sai ya mata shiru ta ɗan sake haɗe fuska shi baya son shiru amma ya ƙware a yi wa mutane banza, sauƙa tayi ranta ba daaɗi su Abeeha har sun shige ita yanzu ina ta nufa ba zuwa ta taɓa yi ba ganin a kyau da tsarin shi ya bambanta da wanda suke zuwa da Abeeha. Wayanta ta duba don ta ƙira Abeehar ma ta ji inda suke su tafi da ita taga katin ta ya kare ta ɗan yi taku biyu tana furta "Oh! ashe ba ni ma da katin, to yanzu ina zan yi??" A karye tayi maganan tana sauƙe hannunta ƙasa, babu zato babu tsammani taji ya sanya hannunshi na dama cikin nata na hagu ya gimtse, da sauri ta kalleshi kaman ba shi ba dole ta fara Binshi sun zaga sossai har wurin kayan makaranta ta ɗauki duk abinda take so suka dawo wurin turaruka ya ɗauki turarenshi ita bata bukatar komai don kayan aurenta duk babu abinda ma ya dauki hanyar ƙarewa suna nan set set, a wurin biya suka ga su Abeeha. Abeeha da ta hange su daga nesa ta taɓa jannah "Addah Jannah kalli ki ga...!" Jannah ta waiga tana kallonsu suna tahowa sun yi matuƙar kyau da dacewa fiye da yadda baki zai fasalta, da sauri ta ɗaga wayanta ta fara musu hoto tana murmushi ganin zai ɗagota tayi saurin sauƙe wayan tana cewa Abeeha "haƙiƙa ba ƙaramin sa'a Afeefah ta taka ba, samun soyayyar namiji irin Ya Rayyan....Ya Allah i just can't imagine.." With so much excitment tayi maganan. Abeeha ma tace "Wlh shima yayi dace Mata Kaman Afeefah are very rare sun dai dace kawai duk su biyun they Look so breathtaking" Gab da su ya saki hannunta ya zaro Atm ya biya aka hada musu komai nasu suka nufi mota, bayan ya shiga ya kunna Ac ɗin sai yaji baya ba da iska kaman gas babu tsaki mai ƙarfi ya ja ya kunna motar suka fice yana sauƙe glass a hankali. Kwanciya tayi ta lumshe ido jikin kujera tana sauraron dukar da zuciyarta ke yi, hannunta da ya riƙe throughout ta kaishi fuskarta ta shafa tana sake sniffing kamshin da ya bar mata har lokacin tana jin softness na hannun cikin nata, bata san sun yi nisa ba sai da suka zo last danger na ɗaukar hanyar gidansu ta ɗan buɗe idanu sai taga wasu maza a cikin napep suna kallonsu kaman an ce ya kalli wurin ya sake jan tsaki ya miƙa hannu ya dage glass ɗin ɓangaren ta har sama, ta ɗan kalleshi bai ko kalli inda take ba ana sake su yayi kwana zuwa gida. A yanzu bai ɓata lokaci ba don idan ya tsaya batawa zai iya makara gashi takeoff din nasu 12 ne dot. Wurinta ya fara shiga tana zaune kawai ta ganshi ta miƙe tsaye. "Zan tafi." Tayi mamaki kwarai don ita yana kasheta da mamaki a tsakankanin. "Allah ya tsare ya ba da sa'a ya kuma dawo da ku lafiya." Ya amsa da Ameen a kan lips ɗin shi yana kallonta. "Ina fata kina sane da jiya ba yau ba ne, bana son yadda kike fita school anyhow make sure kin saka ko hijabi ko ma Abaya before going in ya so in kin isa ki cire, just focus on abin da ya kai ki. Ki kula sossai don ina da matuƙar kishi akan abin da nake so." Yana kai nan ya ajiye mata bundle na 1k guda biyu a kan gadon ɗakin ya juya ya fita. neman faɗuwa tayi ta samu wuri ta zauna tana jin kalaman nashi na dawo mata "Kishi akan abin da yake so? Waye yake son?" Da sauri taje gaban madubi tana kallon kanta sai ta girgiza kai ba dai ita ba kila bata ji da kyau ba ko kuma kariyar nashi irin na ya da kanwa ne. Jikin Window taje ta tsaya tana kallonshi yana magana da duka ma'aikatan gidan sama da mintuna biyar kan ya shiga mota wanda ba ma dashi suka fita ba ya ja ya fice daga gidan, saƙon Shigowar message taji ta janyo wayanta sai ta ga kati ne mai yawa aka saka mata ta kama baki ta riƙe mamaki na so ya kasheta da ranta data ta kunna sai taga hoton da Jannah ta ɗauke su ne ta turo mata sossai hoton ya mata kyau har bata san ta saki kyakyawar murmushi ba tana shafa fuskar wayan... 🖤Gureenjoh🖤 HAIHUWA DA HANJI (A True life story) Fatima Muhammad Gurin (Gureenjoh) Wattpad-Gureenjo6763 Arewabooks-Gureenjoh ADABI WRITERS ASSOCIATION *FREE BOOK* *44* *Laamu Fombina – Daular Gabas* A yankin kudu maso gabashin ƙasar Arewa da bafulatani kai tsaye ke ƙira da Fombina bature kuma ya ce Southland, an yi wata Daula mai kafaffen tarihi da kuma mulki wacce ta samo asali tun daga jahadin Ɗanfodiyo ta hannun ɗalibinsa Muhammadu (Modibbo Adama) tsakanin shekarar 1809-1847. Mafi akasarin mutanen wannan yanki Fulɓe ne ko kuma a ce musu Fula suna daga cikin manyan ƙabilun Africa musamman a yammacin nahiyar. Asalin su yana da matuƙar zurfi, masana tarihi sun taɓa jayayya kan inda suka fito amma dai an fi karkata kan manyan ra'ayoyi guda uku. Ra'ayin Africa ta yamma, Yawancin masana sun ce Fulani 'yan asalin yankin Senegal ne da Mauritania, daga nan suka bazu zuwa Nijar, Mali, Najeriya da sauran kasashe. Ra'ayin Arewa(Africa ta Arewa), Wasu sun danganta asalin su da yankin Masar ko Sudan, suna ganin sun shigo cikin Sahara tun zamanin da. Ra'ayin haɗe da larabawa, wasu sun danganta asalin su da haɗewar 'ya'ya tsakanin mutanen Africa da Larabawa, musamman saboda musulunci da kuma tsananin tsarkin jini da suke riƙewa. Gaskiya kusan duka Fulani Musulmai ne, tun da musulunci ya shiga Afirka ta Yamma ta hanyar su. Sun taka rawar gani wajen yaɗa addinin Musulunci musamman Shehu Usman dan Fodiyo wanda ya kafa Daular Sakkwato a karni na 19. Fulani suna da ɗabi'u da al'adu na musamman da suka bambanta su: 1. Rayuwar Makiyaya (Nomadic / Pastoral Fulani) Mafi shahara a duniya saboda kiwon shanu. Suna yawo daga wuri zuwa wuri suna neman ciyawa da ruwa. Wannan ya sa ake kiran su Bororo'en. 2. Fulani Masu Zaune (Settled Fulani) Su ne suke zaune a birane da kauyuka, suna noma, kasuwanci da neman ilimi tare da yaɗa ta. Su ake kira Fulbe Na'i ko Fulbe Gidda. 3. Mutunci da Tsarkin Jini (Pulaaku) Pulaaku shine tsarin dabi'a da falsafar Fulani. Kuma suna da ababen sha'awa da suka kunsa wanda sun haɗa da: • Munyal (hakuri) • Semteende (kunya da ladabi) • Hakkilo (hikima) • Ngorgu (jarumtaka). A ƙarƙashin wannan yanki da mutanenta suka kasance rabi da kwata Fulani (Pulaaku) aka kafa Masarautar fombina, masarautar tana ƙarƙashin Lamidon farko ta ƙasar Modibbo har wa yau da jininshi ne ke mulkarta, ya kasance daga ragowar daulolin Fulani da suka wanzu tun daga Usmanu Ɗanfodiyo. Ƙatuwar masarauta ce da idan na tsaya misalta muku girmanta da kyawunta zamu kwana muna abu daya bamu gama ba. Cikin Masarautar gari ne guda da ke ɗauke da ɓangarurruka daban- daban kama daga kan Fada, ɓangaren sarki da iyalinsa, Galadima, madaki, wambai, Turaki, Makama sarkin faɗa, Sarkin yaki da ma kowani mukami mai matsayi da ƙima a sarauta, inda kowa sashinsa ke tareda nasa iyalin daidai matsayin kowa. Kuyangu, bayi da Fadawa ma nasu gashin kan suke ci a Sashukansu na musamman inda suke gudanar da rayuwarsu bayan sun taso daga wurin ayyukansu na yau da kullum. Kitchen kuwa fankacece suke dashi inda ake general abinci a kai wa kowani ɓangare nasu dukda kuwa kowani ɓangare akwai kitchens ciki. Akwai asibiti mai zaman kanshi cikin wannan masarauta da ma'aikata ƙwararraru akwai kuma Makaranta da aka yi musamman sabida ma'aikatan masarautar da iyalansu dake amfanuwa. Kodayaushe kashigo Masarautar za ka samu ko wani ɓangare ana hada-hada ana kai kawo. Fadawa na fada, kuyangu da bayi na wuraren ayyukansu, Dogaraye na aikin ba wa Masarautar tsaro dare da rana ayayinda Masu Masarautar daukansu ke aiki ka'in da na'in wurin ganin sun kawo cigaba a Masarautar da al'umman gari baki daya. A zamanin nan da Garkuwa da mutane ya zama ruwan dare a wasu yankunan, abu ne da kan tada hankali kuma matsala ce ga kowani zamantakewa da tsaro, babu ƙabila ko yare, babu namiji ko mace, babu babba bare yaro haka ta shigo cikin wannan Daula ta Fulani ta kutsa kai har cikin masarautar saboda an wayi gari da tashin hankalin garkuwa da Ƴa ɗaya tilo da Laamiɗo Muhammadu Modibbo ya mallaka a wannan duniyar. Wannan matsala ta saka Laamiɗo girgiza har ta kai yana tuna wani al'amari da ya faru a chan baya da ya haddasa ciwon da yake fama da shi a tsaitsaye shekara da shekaru tashi, kasancewar shi nagartaccen sarki, Laamiɗo Mutum ne wanda ya gina al'umma mai gwaɓi, mutum ne da kowa ke rububin ganinshi don agajinshi, Mutum ne da kowa ke son haɗa alaƙa dashi don Arzikinsa. Kyawawan halayensa ya sa ya zamana kowa ya shiga jimami a tare dashi hakan kuma ya ba da gudummawar Gomnati na tura manyan ƙwararrarun sojoji don aiki akan wannan lamari. Ko da Shigowarsu cikin masarautar a Motocinsu saboda an fara isar da su fada ne domin su huta su kuma fara bincike daga tushe, Rayyan ne ya zama na ƙarshe wanda ya buɗe murfin motar sanye yake da full khaki na sojoji fuskar nan kaman ko yaushe a matuƙar haɗe Dukda ma idanunshi masu ɗaukar hankali da kuma karan hancinshi ne ya bayyana kasancewar akwai facemask maƙale a fuskar tashi, yana ajiye ƙafa kan daɓen ƙasan masarautar Wani irin guguwa mai ƙarfin gaske da ƙura ya fara tashi a take wani kalar sautin kuka marar daaɗin ji ya karaɗe kunnuwan ahalin masarautar har ya kai ga gigita su. "BOƊEJO!" Kusan shine sunan da bayi, dogarai da kuyangi ke ta ambata a ruɗe, BOƊEJO wata macijiyace na gado wacce take da shekaru sama da ɗari tana kuma rayuwa a cikin wannan masarauta kaman laƙani ce na wannan masarauta kuma BOƊJO bata kuka babu dalili ta kan yi sau ɗaya idan yayi tsanani sau biyu a kowani bayan lokaci mai tsawo. Kasancewarta Jajazir a jiki da idanu masu firgici da banda sarki ko magajin sarki babu mai iya arba da ita ya wanye lafiya ya sa aka saka mata suna BOƊEJO dake nufin kalar JA. Wasu da ba ma su taɓa jin irin wannan kukan mai firgici da tayar da hankali haɗe da ƙura mai tsananin duhu ba duk sun ruɗe, a take manyan fada suka ba da umurni mai girma na rufe kowacce kofofin masarautar kar kowa ya fita akwai matsala, abin mamaki BOƊEJO na yin shiru sansanin bai kai ga watsewa ba wani irin kiɗan Serewo (Algaita), Tambin (Ganguna) Da Hoddu (kalangu da sarewa) masu mafisar ƙarfi da daaɗi suka shiga tashi cike da sautin da idan ka ji ka san wannan ba dai mutum ke yi da baki ba, sojojin duk da yau ne karon su na farko a irin wannan yanayin sun yi tunanin ma sumame ne ko wani abu don kukan BOƊEJO babu biladaman da ba zai kaɗawa ƴar hanji ba. Shi kam baya ya koma ya jingina da motar tare da lumshe ido kunnuwanshi na jiye mishi irin rububin da ake da umurnin da sarkin gida ke bayarwa na a binciko duk wani baƙo da ya shigo masarautar a yau ana son ganinshi a faɗa matukar namiji ne da gaggawa umurnin Laamiɗo ne, a take fadar ta zama babu shiga babu fita. Wambai ne ya tuna da su don kusan aikin wambai kenan karbar baƙi da kulawa da al'amuran masarauta da sauri ya taho wurin shugabar tafiyar wanda General ne kuma abokin aiki ne ga Rayyan ba wai shugabanshi ba, hannu ya bashi suka gaisa yana bashi hakurin abin da ya faru da yadda aka manta dasu, General ɗin yace "Ranka shi dade ai mu ba ƙaramin tsorata muka yi ba da wannan al'amari mun zaci sumame ne ake shirin kawowa hanyar sanarwar taku kenan!" Wambai na murmushi mai nauyi da ma'ana mai tarin yawa yace "Wannan kuka da kuka ji na macijiyar gadon wannan masarauta ce ta kan yi kukan nan a duk ranar da aka haifi Ciroma wato magajin sarki, haka ma wannan kiɗan kalangun kayan kida ne da suke zaune sama da shekara da shekaru da kansu suke buga kansu a duk ranar da aka haifi ciroman wannan masarauta." Yana musu iso suka fara takawa zuwa ciki tunda ƙurar ya lafa sossai General ɗin yace "Toh Masha Allah, an samu ƙaruwa kenan?" "Ko kuma nesan da muka jima cikin tsumayi ta matso kusa ba, bismillah ku zauna za'a kawo muku ruwa" Zama suka yi bai ba General din damar sake magana ba ya fice. Laamiɗo dake tsaye har yanzu tun fara kukan BOƊEJO ne jiri ya kwashe shi ya tafi zai faɗi a sadda Sarkin ƙofa ya zo ya tabbatar da ba baƙin da suka shigo masarautar a wannan lokacin Galadima yayi saurin tare shi. "Allah rene (Allah ya baka kariya) bi a hankali, Sannu!" "Galadima ka fa ji kukan BOƊEJO ka ji kalangu taya za su yi motsi a banza tsawon shekaru talatin da ɗaya kenan basu yi kuka ba, dole ku je ku nema min Ciroma wlh shi ne!" Dukda a hankali yake maganan kusan kowa a fadan na ji don sun yi tsittt ne, sun san ba lafiya ya cika ba a kwanakin sannan rabon da yayi dogon magana haka tun da aka sanar da shi ɓatan Gimbiya Aissatou(Aisha, na yi pronouncing yadda Fulani suke pronouncing ne). Turaki ne da aikinshi ya zama ba sarki shawara yace "Allah sene (Allah ya yalwataka da farin ciki) ko za'a bincika cikin baƙin sojoji da suka taho wannan ƙasa tamu? Don da alama baƙin cikinmu ne ke gab da yayewa." Tsam ya miƙe a take dogaran da suke tsaye gefen hagu da damanshi suka fara jefa kirarin "Gyaaaaraaa kintsi da kyau..! Taka lafiya mai talakawa" "wambai kaini wurinsu" "Allah ya baka yawan rai ba za'a yi ƙir...!" Hannu kawai ya ɗaga mishi, a take manyan fada da duk suke tsaye suka rufa musu baya don tuni wambai ya shiga gaba. Yalwataccen parlor ne mai cike da kayan alatu na sarautar zamani, an cika gabansu da tarin kayan itacuwa da ma ababen alfarma har da su ɓiradam ɗanyen tatsa, sun yi nisa da ci amma shi kam yana zaune ne kawai idanunshi zube a wuri guda, fuskarnan tayi ja idan ka zuba mishi idanu za ka fahimci baya cikin natsuwarshi don karfin hali ne ya ajiye shi wurin. "Gyaaara kintsi da kyau..!" Da ke ta ƙarato su ne yasa suka fahimci kaman mai martaban ne da karan kanshi ya taho hakan ya sa duk suka miƙe tsaye, General ɗin ne ya taɓa Rayyan hakan ya sa shima ya miƙe ya mayar da kanshi ƙasa yana jin yadda zuciyarshi ke tseren gudu, Laamiɗo ya shigo parlorn tuni kwarjini da girman matsayinshi ya saka su sake natsuwa, tsabar yadda yake jin a lokacin zai iya mutuwa idan bai yi ido huɗu da cikar Muradin shi ba binsu ya fara yi ɗaya bayan ɗaya yana kallon fuskokin su, jikinshi har rawa yake idanunshi sun cika tafff da kwallar marari da bege. A lokacin da ya iso kan Rayyan ya tsaya kawai yana kallon irin tsawon Fulani da yake dashi, bambancin ya gina jikinshi hakan ya ɗan rage mishi tsawon kaɗan amma Dukda haka ya ma kere Lamidon da kaɗan. "Babana!" Laamiɗo Ya faɗa cikin wani karyayyen murya yana kai hannunshi ya dafa kafaɗar Rayyan da ya saka shi dolen ɗago idanunshi da suka cika da kwallah masu zafi suka haɗa idanu. Jiri ne ya kwashi Laamiɗo ya tafi kaman zai faɗi tsabar wani abu da ya dake shi sai Rayyan yayi saurin sa hannu ya tare shi yana ɗaga idanunshi sama don hana hawayen shi zuba amma inaaa sun riga sun taho, Laamiɗo ya fusge facemask din dake fuskarshi cikin harshen fulatanci yake cewa "Babana kaine? Da gaske kai ne a gabana? Sameeer..." Za ka iya fahimtar ruɗu, farin ciki da tarin damuwa duka a cikin Muryar tashi. A hankali Rayyan ya ce "Abeey!" Sai Laamiɗon ya rungumeshi shi kuwa ya ɗora kanshi a kan kafaɗar shi yana barin hawayen shi zuba cikin wani irin yanayi marar fasaltuwa, tuni jama'ar parlorn suka fara fita sai da aka watse tas aka bar su su biyu kachal rungume da juna, kan kace kobo kunnuwan masarauta sun fara aiki inda sashe sashe, bayi bayi, kuyangi kuyangi ake ta zancen dawowar Ciroma Sameer Muhammad Modibbo cikin masarautar bayan shekaru ashirin da shidda da ɓacewar shi. Babbar macece mai cike da wani irin izza da ƙasaita da kana kallonta sai gabanka ya faɗi, bata da fara'a ko na miskala zarratin haka komanta tana yi ne cikin isa da wani irin mulki da ta saba shimfiɗawa cikin masarautar shekaru da dama, Fulani Adama kenan uwargida ga Laamiɗo kuma uwar ɗakin duk wata mace da zata shigo gidan ko a mata ko a kwarkwara tana da irin izza da har kan ba mutane tsoro, ga kafaffen zuciya da salo salo wurin shimfida mulkin son rai da samun duniya a tafin hannu. Jeka-ka-dawo take a tsararren falon nata, sanye cikin shigan alfarma da kamshi na musamman tun kukan BOƊEJO na farko taji kaman an tsire mata zuciya ne hakan yasa ta kasa zaune ta kasa tsaye, duk wani abinda zai hana Fulani Adama natsuwa ba ƙarami bane, Shigowar Amintacciyarta da gudu yasa tayi hanzarin Juyowa tana zuba mata firgitattun idanunta masu kaɗa 'yar hanji. "Allah ya ja kwanan Fulanin Laamiɗo, farin ciki masarauta, Uwargida kuma hasken zuciyar Laamiɗo uwar yarima da yardar..." "Bana son ɓata lokaci Menene ya faru? An yi baƙi ne? Me ke shirin faruwa ne Balki?" "Gobara daga kogi ranki shi dade..." Baya baya tayi ta kai zaune cikin tsadaddun kujerunta hannayenta duk biyu dafe da Goshi. A chan wani tsararren sashe cikin wasu kujerun alfarma Fulani Faɗimatu ce zaune fuskarta Jajazir idanunta har sun jirkice Dukda tsaf take cikin shiga ta alfarma da ƙawa kallo ɗaya za ka yi mata ka san cewa ba ta cikin natsuwar ta kukan BOƊEJO kaman ƙara mata damuwa cikin damuwarta yayi don ta gigice ta kasa zaune ta kasa tsaye a sadda Kuyangarta ta shigo ta zube ƙasa "Allah ya kara miki lafiya da yawan rai, Allah ya kare gabanki da bayanki" "Menene kande? Me ke faruwa?" "GIZO BA YA HANA RUWA GUDU...! Zakarar da Allah ya nufa da chara..." Dafe zuciyarta tayi tana fashewa da rikitaccen kuka mai tsuma rai. 🖤Gureenjoh🖤 HAIHUWA DA HANJI (A True life story) Fatima Muhammad Gurin (Gureenjoh) Wattpad-Gureenjo6763 Arewabooks-Gureenjoh ADABI WRITERS ASSOCIATION *FREE BOOK* *45* "Babana...Sameer ka gane ni?" Laamiɗo ya faɗa har lokacin gani yake kaman mafarkin da ya saba ne yana motsawa zai iya ganin Rayyan ya ɓace, rauninshi ne ke sake bayyana a gaban dattijon wanda dama tun yaranta shi ne mutum ɗaya jal dake ganin hawayen shi sai Baba Maudo wanda ke matsayin Galadima kuma ɗan uwa na jini ga mahaifiyarshi. Hannun Abeey ya riƙe ya zaunar da shi tare da yunkurawa ya kai ƙasa kan gwiwowinshi gabanshi kanshi a ƙasa a hankali ya furta "A gafarceni taƙawa" Riƙo hannunshi Abeey yayi ya ɗago shi ya zaunar dashi gefenshi yana jefar da duk wani formalities na sarki don a yanzu uba yake. "Da gaske ne kenan..! Kai ne da gaske nake gani Sameer? Ina ka shiga ka manta da asali? Me ya fitar da kai daga cikinmu ya nesanta ka? Wani irin rayuwa kayi a wani wurin da babu mu har zuwa wannan lokaci Sameer? Na yi nema! Na yi nema har yau ban fidda ran ganinka ba ashe da rabon sake ganinka kafin in bar duniya!" Yana maganan yana ta duba jikinshi ko zai ga wani alamun wahalar rayuwa amma ya ganshi fes kuma fresh don ko daga tafin hannunshi da ya riƙe ya fahimci yana cikin hutu da jin daaɗi Dukda haka sai da ya tambaya zamanshi Uba mai cike da yunwar ganin ɗan shi namiji ɗaya tilo da ya mallaka a duniya. "Abeey ka kwantar da hankalinka don Allah, ni ne! Sameer ne a idanunka ba zan jefar da sunan da ka yi min yanka ba sai dai Rayyan ne a idanun duniya wanda shi ne sunan da hasken rayuwata kuma wacce ba ni da kamarta a wannan duniya ta bani... Abeey Aisha tana chan hannun azzalumai shine abin da ya kawo mu duk wannan za mu yi daga baya na tabbatar Abokan aikina suna chan suna jira na" Kallonshi kawai Abeey ke yi yadda yake jera maganan da rashin cikakken fara'a mai tsanani da ya kamata ya gani a fuskarshi. "Aisha na da muhimmanci kwarai kasancewarta mace cikin miyagu amma kai ma kana da muhimmanci Ciroma... Mahaifiyark.." Da sauri ya katse shi "Abeey...!" Sai yayi shiru don bai saba katse maganan mai martaba ba, duk jimawanshi wani wurin an haife shi ne cikin masarautar kuma ya tashi da horo mai tsanani da kuma jarumta na asalin 'ya'yan sarki waenda ake musu mafarkin sarauta a gaba don haka yana sane da komai bai manta ba. "Abeeyy ka yi haƙuri ka gafarceni ka bar maganarta for a while ina cikin farin cikin ganinka cikin koshin lafiya, adu'ar da nake ta yi kenan duk ranar da zan riskeka in riskeka cikin lafiya da kuzari in ga wannan farin cikin dake shimfide bisa kamilallayar fuskarka, ka haske ni da annurinka, ka cika ni da kwarjininka ka min hirar tarihin Fulani masarautunsu da ma al'adunsu..." Muryarshi ne ke rawa ya mayar da kanshi ƙasa yana datse harshe don kuka ne ke zuwa mishi mai ciwo, shi kaɗai ya san irin raɗaɗin kewar mahaifinshi da yayi a wannan duniyar, shi kadai ya san irin halin da ya shiga na rashin shi kusa dashi ba tare da ya bari damuwar shi ya fita fili ba don ya san shi aka fi cuta, an cutar mishi da mahaifi ainun da baya tunanin zai iya yafe wa. Mai martaba ma hawaye yake zubarwa, amma fahimtar wani abu da yayi ya sa bai iya sake magana ba suka yi shiru. Chan da ɗan jimawa ya ce "Aisha! Ta ya ta ɓace Abeey?" "Makaranta suka tafi da 'yar uwarta Zara'u akan suna da jarabawa dake ƙaratowa za su kai yammaci Dukda sun san ban yardar musu kaiwa dare a waje ba Fulani Adama ce ta ba su go ahead a kan za su dawo ba tare da na sani ba hakan ya sa suka yi dare har wannan al'amari ya faru anan yankin makarantar tasu dayake daga su sai Driver shima a raunane yake yana asibiti kwance" "In shaa Allahu za mu tabbatar babu abinda ya same ta, lafiya za ta fito." "Ku tabbatar da hakan Ciroma. Allah ya taimaka amma za ka dawo ko?" Ya kalli Abeey. "Zan dawo ko don saboda kai Abeey..." Kallonshi kawai Mai martaba yake yi yana ayyana abubuwa masu dumbin yawa a ranshi. Ya girgiza kai "Ba saboda ni ba dole ka dawo Sameer saboda al'ummarka da suke jiranka dole ka dawo saboda ba zan iya cigaba da nesanta da kai ba tunda Alhamdulillah kana raye cikin koshin lafiya." Ba tare da ya ɗaga kai ba ya ce a hankali "Wannan magana ce mai tsawo ranka ya dade ya kuma ba ka yawan rai, ina da family ina da kanne da suka dogara da ni sannan ina da Mata duk basu san wanene ni ba..." Murmushi mai ciwo mai martaba ke yi duk Sameer ya taka waennan matsayi har ya kai ga Auren wata a waje ba Zara'u da aka bashi tun daga ranar da aka haife ta ba, yana da wasu zuri'ar da suka zama priority a gareshi da har bai iya ɓoye wa ba hakan ya sosa mishi rai ainun haƙiƙa ba zai bar duk abin da ya nesanta shi da Sameer ya sha a banza ba, Sameer dake da sunan babanshi amma yake ture sunan yake makala Rayyan bayan ga asalinshi, da kyar ya hadiye wani abu mai ɗaci "Ina jiranka Ciroma, zan jira har ka dawo da ƙanwar ka cikin gidan nan daga nan za mu ɗora" Kai Rayyan ya gyaɗa suka sake yin shiru na tsawon lokaci kan mai martaba ya miƙe tsaye Rayyan ma ya miƙe kanshi ƙasa ya furta "Allah ya baka yawan rai ya ƙara maka lafiya da imani!" Kai kawai mai martaba ya gyaɗa bai ce komai ba ya fice dogarai dake bakin kofa suka fara zabga kirari har ya wuce. Rayyan ya ɗauki facemask ɗin shi ya mayar, ya zare bakin shade dake gefen aljihunshi ya saka ya gyara hulanshi ya fito daga parlorn, yana bayyana a waje hadimai da dogarai suka shiga zubewa. "Allah hokke jam (May Allah give you peace) Ciroma Sameer ɗan Laamiɗo jikar Modibbo... Girman ɗa gado, Ɗan sarkin da ya san Allah, Ɗan sarkin da yayi haƙuri Ɗan jarumi gadon jarumta Ruwan sanyi mai dafa ganda... Murucin kan dutse baka fito ba sai da ka shirya Gobara daga kogi magani naka Allah, Damisa ba'ai maka kallon banza, sarauta dole in babu ku gari ya watseee.." Sossai ya sake kamewa wannan jinin na sake bayyana kanshi da kanshi, takawa yake kaman ba zai tafi ba cikin sarauta har ya isa ga motar sauran sojojin da suke jiran shi da kallon mamakin al'amarinshi musamman waenda suka san shi su ke Binshi bai cewa kowa komai ba daga hadiman har sojojin ya shiga ya zauna suka fice daga fadar. Kai tsaye mai martaba sashen Fulani Faɗimatu ya nufa dayawa suna mamaki don baya zuwa sassan matan sai dai su suje amma sun mishi uzuri kasancewar sun san iyaye ne da suke cikin murnar bayyanuwar ɗan su namiji tilo, wasu daga cikin gulmammu har an fara tambaye tambayen Meyasa bai je ga mahaifiyarshi kuma ya bar masarautar? Wasu na ganin barin shi da Laamiɗo yayi ya tafi ganganci ne. Tana zaune har lokacin kuka take ta fara jin sanarwan zuwan mai martaba sashen ta, da sauri ta miƙe tsaye daidai yana shigowa ya tsaya ya zuba mata idanu yana kallonta chan ya ce "Faɗimatu Me kika aikata?" Kanta ta mayar ƙasa tana sake sakin kuka cike da tarin nadama da kunyar mai martaba. "Ashe kukan nan da kike shekara da shekaru ba na rashin ɗa bane sai na yunkurin lalata rayuwarshi? Me na miki da kika zaɓi azabtar da ni da hannayenki Faɗimatu? Me na miki da kika zaɓi gani na cikin ciwo da azabar rashin ɗa tsawon shekaru ashirin da shidda? Me kika mishi da ko magananki baya ƙaunar ya ji anyi? Kin san zuciyar bafulatanin da aka hasala?? Kin san yara nawa ne da zuciya ya dibe su suka tafi tafiya na har Abada sun ki waiwayan baya? Ba sai na faɗa miki ba kin san wanene Bafulatanin mutum... Amma ina so ki san abu ɗaya na gode Allah da ya amsa min adu'ar dawo min da Sameer ba zan taɓa mishi dole ya kalleki ba idan baya so..alhakin mu da kika dauka kuma wannan tsakanin ki da rabbissamawati" Sossai take kuka tana girgiza kai, mai martaba masoyinta ne in ta ce bai kaunaceta ya ɗaga darajar ta cikin mata da kwakwarayenshi ba ta yi ƙarya, duk wata kulawa ya bata ya tausaya mata dukda yana cikin damuwan shima amma ya rarrasheta a lokacin da yake tunanin za ta fi shi jin zafin ɓatan danta, kwarai ta fishi ita da bata san inda yayi ba bayan nan ita da alhakin shi ke maƙale a wuyanta na tsawon wannan shekarun zuciyarta bai huta ba, idanunta basu tsagaita da zubar kwallah ba. "Ranka ya daɗe ka gafarceni, ka tsaya ka saurari uzurina don Allah..." Ɗaga mata hannu yayi "Ba ki da uzuri Faɗimatu baki dashi..! Babu uzurin da zai wanke bakin cikin da nake ciki a yanzu you were the last person i've expected that from, am very disappointed..." Katsewa magananshi yayi jin sanarwar isowar Fulani Adama, da kuka ta shigo "Alhamdulillah! Alhamdulillah!! Allah mun gode maka ya Allah da ka share mana hawaye ka amsa adu'ar mu ashe Magaji na raye? Ashe muna da rabon sake ganawa? Mai martaba sashen ka nayi don wannan babban abin murna ne sai ake sanar min kana nan ashe... Ina yake? Ina Sameer in ga yadda ya sauya ya zama mutum cikakke?" Har yanzu idanunshi da suka sauya suna kan Fulani Faɗimatu kan ya janye ya kalli Fulani Adama yace "Alhamdulillah yana nan lafiya Fulani, a yanzu ya tafi abinda ya kawo shi wato tseratar da kanwanshi." "Alhamdulillah! Ashe rayuwa ya inganta Soja ne ashe?" "A sojojin ma ba laga-laga ba. Na bar ku lafiya" Yana kai nan ya juya ya fice. Ta kalli Fulani Faɗimatu tana murmushi "Barka na taya ki murna Faɗimatu" "Ai ke ce uwa a gareshi Fulani ke ya kamata mu taya murna.." "Kwarai kuwa! Gashi ya zo a gaɓar da matarshi ma ta isa aure gwara da muka jinkirta aurar da zarah ashe alƙawari zai cika" Kai ta gyaɗa bata iya tace komai ba don a gigice take, ta sake murmushi tana ta kallonta kan ta juya ta fita, zubewa Fulani Faɗimatu tayi kan kujera bata zaci lamarin zai kai haka ba, kuruciya ne da buƙatar uwa na ganin ta ba abinda ta haifa kariya ya sa ta aikata bata zaci abin zai zama mata haka ba sam, tun daga ranar take nadama har yau. Ko motsi bata sake yi ba sai ga Fulani Aminatou itama murna ta zo tayi mata bata kai ga fita ba sai ga Fulani Salimah itama ta mata murna duk amsawa take amma tana sane da wanda ya kai ciki da wanda bai kai ba Dukda duk yanzu ba sune gabanta ba. Duk rubibin da ake Madaki da Makama suna zaune ne tamkar a kan ƙaya fata kawai suke sarki ya ce ya sallame su su samu su keɓe aiko Galadima na sanar da tashin Fada kai tsaye su biyun ganawa suka nemi yi da Fulani Adama. "Balki ki sanar da su ba yanzu ba da kifi ya riga ya ruɓe su bari sai ya daina wari za mu tattauna" Da sauri amintacciyarta bilki ta amsa "an gama Allah ya baki yawan rai" Tana kai nan ta fice taje ta kai saƙon suka kalli juna suka juya suka tafi babu mai uhm bare uhm uhm. **** Shi kam Rayyan komai ya watsar suka shiga kokarin ganin sun tsara yadda za su kubutar da su Aishatu cike da hikima irin ta squad ɗin tasu na musamman da aka turo wannan aiki, lokaci lokaci ya kan yi tsaki kaɗan har dai aka gama kuma akwai alamun nasara don sun samu haske sossai daga ƙiran da aka yi na biyu. Bayan sun gama zaman ya nufi ɗakinshi kai tsaye wanka yayi saboda gajiyar da yake ji ainun jikinshi, ya fito ya shirya cikin kayan baccinshi ya nufi gadon ya kai kwance kaman jira ya fara jin ta jikinshi, emptiness da bai san na menene ba ke ratsa shi ji yake gadon yayi mishi faɗi ƙwarai, shafa cikinshi yayi da bai ci komai ba tun safe da tana nan da ta fara mishi puppy face tana roƙon shi ya ci wani abu wane cikinta ne tsintar kanshi yayi da ɗan murmusawa a fili yace "Yarinyar ta cika tsoro" Yana maganan yana tuna idanunta in ta ji muryarshi ko idan yayi mata tsawa. Daga karshe da ya ga ba zai iya bacci ba dole ya tashi ya sha coffee ya koma ya kwanta ya janyo wayanshi ya tafi numbern ta da ya karɓa da safe kawai ya yanke bin shawarar zuciyarshi na ko muryarta ne yaji ya danna wa ƙira. Tana kwance tun tuni ko shirin bacci bata yi ba, takardu ne gabanta amma ta kasa karatu sai tunaninshi take ya je lafiya? Ya ci abinci? Sun fara aikin? Ta rasa natsuwa duk adu'arta na salollin yinin akan Allah ya kare mata shi ne ya bashi sa'a a duk abinda ya sanya gaba, tana nan tana juye juye a kan gadon sai ga ƙiran shi bata san Layin ba don bata dashi. "Waye ke kirana ƙarfe sha ɗaya?" Tayi tambayar tana sake kallon lokaci kaman ba zata ɗaga ba ta zo dagawa ya yanke, ya sake ƙira karo na biyu dole ta ɗaga ta makala a kunne bata yi magana ba shima sai bai yi ba suka yi shiru suna sauraron numfashin juna, chan tace "Waye ne? Meyasa ake kira a irin wannan lokaci?" Ya tsinci kanshi da wani kalar murmushin da bai fi second biyu ba, ashe ta iya tsiwa shi ne take yi wa puppy eyes na tsoro. "Idan babu abin faɗa zan kashe don ina da abin yi..." "Ba ki iya sallama ba?" Daram gabanta ya faɗi tayi saurin Miƙewa zaune tana sake riƙe wayan da kyau Ya Saraki ne, tuna abin da ta faɗa da farko yasa tayi saurin cewa "Kayi haƙuri ban san kai ba ne Assalamu Alaikum warahmatullah" Ya amsa sallamar "Me kike yi ba ki yi bacci ba har wannan lokaci?" Ta kalli takardun gabanta tana mamakin yadda ya ƙirata har yana ɗan magana Dukda maganan kaman za'a yi kaman ba za'a yi ba yake jefowa. "Abu nake yi ne shiyasa ban kwanta ba." Shiru yayi idanunshi a lumshe yana sauraron muryarta. "Abin babu suna?" "Karatu!" Ta amsa suka ɗan yi shiru ita dai har hannayenta sun haɗa zufa nervousness da kyar ta fitar da abin da ke ranta kan yayi magana ta ce "ka isa lafiya?" Buɗe idanunshi yayi ya zubawa wuri guda Mammi ce ke faɗo mishi a duk sadda motsin yarinyar nan ya shige shi sai ya rasa Meyasa yake tuna Mammi, yanzu haka abinda yaji Allah ne kadai ya sani. Mammi ce kaɗai duk inda zai je sai ta tabbatar da isan shi lafiya, ita ce yake yawan jin wannan kalmar daga Bakinta ba wata ba. Jin shirun yayi yawa tace "Hello!" "Lafiya! Ki ajiye abin da duk kike ki kwanta" Ta amsa da Toh "Kar ki kashe!" Chak ta tsaya da yanke call din ya ɗan kausasa murya "Ke kika ƙira ne da za ki kashe?" Ta haɗe lips ɗinta shi dai ba'a yi mishi ba za'a zauna dashi a wanye lafiya ba. "Afuwan" Ta faɗa chan ƙasa a hankali da ya saka shi sake lumshe idanu. Miƙewa tayi da wayan a kunne ta tattare duk takardun ta saka a speaker kar yayi magana bata ji ba ta shiga uku ta chanza zuwa kayan bacci ta kashe wuta taje ta hau gado. "Na gama." Duk motsinta yana ji. "Ba kya alwala ne idan za ki yi baccin?" "Manta wa nayi!" Bai ce komai ba taje tayi alwalan ta zo ta zauna tayi Adu'a ta shafa duk yana jinta kan ta kwanta tayi shiru. Bacci ne ya ci karfin idanunta don bata saba hira ba saboda bata yin baccin da safe ko rana ta riga ta saba tun chan. Cikin Muryar bacci tace "Sai da safe ya Saraki" Ya ja numfashi a hankali don Muryar ya isa inda bai kamata ya isa ba, yana sauraron komai har tayi bacci kan ya katse ƙiran ya ajiye wayan kan kirjinshi da kyar baccin ya ɗauke shi cike da tunanunnuka. 🖤Gureenjoh🖤 HAIHUWA DA HANJI (A True life story) Fatima Muhammad Gurin (Gureenjoh) Wattpad-Gureenjo6763 Arewabooks-Gureenjoh ADABI WRITERS ASSOCIATION *FREE BOOK* *Masu tambayar daga farko a yanzu za ku yi haƙuri ku jira a ƙarasa don abin da ya saura babu yawa sossai a haɗa doc ayi distributing gabaɗaya because pages almost 50 ba abu bane mai sauki in ta forwarding please bare with me* *46* Kwanakin da suka biyo baya sun zo mishi da tarin ayyuka haɗe da zirga-zirga ta yadda ma wani daji suka koma suka yi camping don dai ganin an ceto su Aisha a hannun waennan Ƴan garkuwa da mutane, inda yake ko service babu hakan ya sa ya manta rabon da su yi waya ko da Abeeha ce kuwa bare Afeefah da sau biyu ya taɓa kiranta gashi har an ci tsawon sati uku suna abu ɗaya ba su ƙare ba, sun yi namijin kokari duka team ɗin wanda suka hada har da taimakon wasu airforce, polisawa da 'yan sa kai da ake cewa Hunters a cikin sati na huɗun suka samu gagarumar nasara bayan kubutar dasu sun kubutar da dayawa daga cikin waenda abin ya ritsa dasu kuma sun samu nasarar hallaka dayawa daga cikin miyagun. A yau da ya kasance Juma'a suka iso cikin garin Fombina zuwa masarauta, kai tsaye aka musu iso don an san da isowarsu kuma an shirya musu tarba na musamman, ko bai nuna ya san Aishan ba ma itama daga ita har Zara da yake a tsorace suke har lokacin ba tantance kowa suke yi ba sai da suka gansu tsakiyar masarauta kai tsaye sashen Uwar ɗakinsu Fulani Adama aka yi dasu ta fito ta rungumesu tana hamdala nan suka saki kukan da ya gama cin su a rai. Shi kam Rayyan na cikin baƙin fada inda sarki ya nemi da su koma masaukinsu su huta kafin ya gana da su ko zuwa dare don yanzu yana ta samun baƙin taya murna daga kananan hukumominshi da na shuwagabannin rugagen dake kewaye da Daular fombina, Rayyan ya tashi zai bi bayansu Laamiɗo yayi gyaran murya ya furta "Ciroma!" Chak ya tsaya, ya dawo da baya ya koma zaune "Allah ya baka yawan rai!" "Bisa tsarin umurnin da na yanke, ka shigo kenan Sarkin gida zai maka rakiya zuwa sashenka an tanadar maka duk wani abin da zaka buƙata ka je ka huta iyayenka na bukatar ganawa da kai." Da wani irin hanzari ya ɗago ya kalli mai martaba sai kuma ya mayar da idanun ƙasa ganin duk idanun manyan fada na a kanshi, Miƙewa yayi "Na barku lafiya!" Daga haka ya fice sarkin gida yayi saurin mara mishi baya, a wajen ma dogarai shidda ya gani sun rufa mishi baya kuma ya san sune aka yi assigning don kare lafiyarshi haka kawai yaji kaman an takura shi. Sashe ne na musamman tsararre ya ji furnitures da komai da komai masu tsada da ɗaukar ido amma shi bai wani burgeshi ba tunda ba tatse ɗin shi bane, ɗakuna huɗu ne a sashen ya nufi wanda sarkin gida ya nuna mishi shine nashi ya shige ba tare da ya ce mishi komai ba yayinda sauran dogaran suka kafe a bakin mashigar sashen. Komai kuwa akwai ko da ya buɗe wardrobe kaya ne kala kala kawai gasu nan, manya da kananu Dukda ya san idan ba a cikin sashenshi ba a yanzu saka kananun kaya ma yayi yawo da su a cikin masarautar ya haramta mishi, kayan jikinshi ya zame ya shiga wanka ya jima sossai kan ya fito ya shirya cikin karamin three quater baka da wata karamar riga fara ta kama shi ta fitar da surarshi na cikakke kuma karfaffen namiji, wayanshi ya zara ya fito parlor sai ya samu an cika dining ɗin da kuloli na alfarma wanda ya san abinci ne ciki. Gyaran murya yayi da hanzari dogarin dake dab kofa ya faɗo ciki ya zube ƙasa "Allah ya ja da zamanin Ciroman fombina, Allah ya kare gabanka da bayanka ubangidana, gaba salamun baya salamun naka faɗa ne namu cikawa...." Hannu ya ɗaga mishi "Daga ina aka kawo wannan?" Ya jefa tambayar yana ɗora kafa ɗaya kan ɗaya a lokaci daya yana dan karkaɗawa idanunshi zube a kan screen ɗin wayanshi "kuyangin Uwar magajin sarki ne suka shigo dashi ranka ya dade...." "Ku tattara ku fitar min, daga yanzu ban amince a shigo min da abincin ko wani sashe ba don ba na buƙata!" Cikin ba da umarni yayi magana hakan ya sa dogarin sake zubewa "An gama sadaukin maza..!" Da wuri yaje ya fara tattare wa shi kam yana zaune shiru don ya gwada Layin Afeefah bai shiga ba na Abeeha kira daya ya mata bata ɗaga ba kuma bai sake kiran ba. Damuwar shi yadda mai martaba ya ba da umarnin dawowanshi kenan ya san ba zai taba amincewa ya tafi ba amma kuma idan ya zauna kaman bai yi adalci ba, bai kamata kawai su Uncle Musa su ji cewa ya dawo gida ba dole yana bukatar komawa da su su san asalinshi ya tattauna da su da tsara yadda za'a tafiyar da rayuwar su Abeeha da yake jin banda aure babu wanda ya isa ya ce zai karbi riƙon Abeehar don kawai ya dawo gida har yanzu shi a jinin Maami yake kallon kanshi kuma a hakan yake so ya tabbata don haka dole ne ma ya ga sarki. Time ya kalla karfe tara ne kwata kwata da mintuna ashirin, Dukda baccin da ya tarar mishi dole yaje ya ga sarki ya san karfe goma zai koma turakarshi don fara shirin tafiya masallaci, Miƙewa ya yi ya koma ɗaki ya shirya cikin wasu navy blue kaftan da ya sha ɗinki irin na sarauta, ya saka hular da ta dace da kayan ya zura takalmi ya fito hannshi riƙe da waya amma sai ya tattaresu ya goya a baya ya fice daga sashen dogaran na ganinshi suka rufu za su bi shi ya juyo ya kalli shugabansu. "Sunanka?" "Gaabɗo ranka ya dade" (Joy yake nufi) "sauran su zauna kai ka biyo ni" Yana kai nan ya juya da sauri Gaabɗo ya bishi har turakar mai martaba duk inda ya ratsa hadimai za su zube suna kwasar gaisuwa kai kawai yake ɗaga musu, sai da aka sanar da isowarshi kan ya shiga, ya ci sa'a mai martabar ma na son ganinshi da kallo yake ta Binshi har ya zauna a ƙasa kaman yadda me martaba ke zaune cikin shimfida na alfarma ya kishingida da tun tun. "Abeey barka da wannan lokaci" "Barka dai Ciroma, na san ka ji hukunci na kuma kana tunanin bai maka daaɗi ba amma abin da zan iya cewa kenan Sameer ba zan bari ko kusa ka sake subuce min ba, Kukan BOƊEJO da ma sautin kalangun gado sun isa su tabbatar maka da cewa kai ne mai jiran gado" Numfashi ya ɗan sauƙe yace a hankali "Abeey ka yi haƙuri da abin da zan faɗa ba zan saɓa umarninka bane amma zuri'ar da na ajiye a chan sun fi karfin na sanar da su cewa na dawo nan a waya, ɗiyar su ta zame min uwa da uban da na rasa a rayuwata tsawon shekaru ashirin da shidda bata taɓa gajiyawa da hidimata ba, bata taɓa min kallon banza ko Harara da sunan tsana ko kyara ba, ta gatanta ni ta fifitani fiye da komai da ta mallaka a duniya ciki har da miji da 'ya'yan cikinta, Abeey duk yadda zan fasalta maka irin son da Mammi tayi min ɓata baki ne duk kuma ta yi bata san ni waye ba har sai da take kwance a gadon mutuwarta a haka roƙona tayi da in dawo in samu farin cikin da na rasa, in dawo in ji uzurin...." Sai bai ce komai ba ya duƙar da kai. Hadiye abin da ya taso mishi yayi kan ya cigaba "Ban shirya dawowan ba na riski labarin ɓatan Aisha bayan ma ƙiran da shugabanmu yayi min na ina cikin team da aka yi assigning wannan aiki na taho ne ba da shirin dawowa b.." "Muhammad Sameer" Laamiɗo ya kirashi runtse ido yayi don ya san bai amince bane. "Ka ba ni labarin abinda ya faru daga barinku gidan nan da mahaifiyarka, na dai san ta nemi izinin tafiya chan mambila wurin dangin mahaifiyarta kuma na bata izini da driver da kuma amintacciyar Kuyangarta sai labari marar daaɗi aka dawo min dashi da sunan ka ɓace a tsaunukan mambila an neme ka an rasa na kwashe tsawon shekaru ban bar kowani hukuma sun huta ba da neman ka har wasu suka zartar da cewa ka mutu ni ban yarda ba hakan ya sa a kullum nake Adu'a duk juma'a nake sadaka duk goman karshe na kan manta kaina ina rokar maka kariya da nasara a duk inda kake da Fatan Allah ya bayyana min kai ya tsare maka imaninka me ya faru? Meyasa daga kalamanka na yarda Ammienka na da hannu dumu dumu akan abin da ya faru?" Kanshi na a ƙasa ya shiga magana kana jin ɗaci a saman harshenshi a kuma hankali yake maganan "Abeey bayan mun yi muku sallama mun bar nan tafiya ne mai nisan gaske muka dauka ba tare da na san inda muka nufa ba, na taɓa zuwa mambila sau ɗaya don haka inda muka nufa bai min kama da hanyar ba, idan nayi bacci na gaji na farka na tambayi Ammie har yanzu bamu isa ba sai ta mayar da ni jikinta ta rungume tace har yanzu da saura ban sani ba ashe nesanta ni take da asalina, nesanta ni take da inda na fi wayo da kuma farin cikina duk ku biyu, yamma ne sossai muka isa inda ban sani ba hatta yaren su kaɗan kaɗan nake ji shima saboda akwai wasu kuyangai dake yi anan ina sha'awar iya yaruka na saka su a gaba ina koyo, ko da ta saka driver tsayawa kuka take yi ta bani ƙullin kayan marmari da abinci waenda basa lalacewa da wuri cikin guzurinmu tace in riƙe, muka sauka muka bar driver da Kuyangarta Kande a mota mun yi tafiya sossai har muka kawo gefen wani juji da babu hada hadar mutane sossai ta kalleni. "Ka yi haƙuri ɗana ina sonka amma dole ta sa zan rabu da kai babu yadda na iya!" A karye na ce mata "Ammie Meyasa tunda muka fito kike kuka? Meyasa za mu rabu? Me muke yi anan?" Ta ja numfashi tana share hawayen dake kara gangara tace mini "Nan shine inda na ji ya kwanta min ka cigaba da rayuwa, ka yi aiki kaman na jaruman maza ka nema da kanka ka samu har ka tsaya da kafafunka, idan da rabon mu gana watarana za mu gana amma a yanzu ka cire cewa kai ɗan sarki ne jikan sarki, ka jingine ka taɓa sanina ko mahaifinka, ka manta ka taɓa ko da amsa suna Ciroma Sameer ka samu sabuwar rayuwa zan maka sdu'a ba zan gaji ba amma daga yau ka gama zaman masarauta..." Hankalina ya tashi da kalaman ta na rikice ina tambayarta "Meyasa Ammie? Me yasa zan manta ku? Meyasa zan manta Abeey?" "Saboda Dole ne Sameer!" Ta daka min tsawar da bata taba min irinshi ba Dukda na razana kuma kuka ba ya daga cikin al'amarina ban san na fashe da kuka ba na riƙo hannayenta ina roƙonta kar ta bar ni anan ban san kowa ba, kar ta bar ni anan ba zan iya rayuwa ba Ammie ta zame hannunta ta tureni har na faɗi na rarrafa ba tare da na damu ba na rike kafarta ina kuka sossai da roƙonta ta tafi da ni amma ce min tayi "Ko a mafarki ka biyo baya na ba zan taɓa yafe maka ba Sameer!" Baya baya nayi na zube a ƙasa a zaune ina kallonta har ta ɓace min, na ji na tsani duniyar na ji na tsani kowa da komai kuma a lokacin zuciyata ta kafe Abeey na ji ba zan iya sake yi mata kuka ba tunda bata so na ta tsaneni, babu abin da yafi kona min rai irin bolar dake gangana nan uwata tace min in ci gaba da rayuwa, nan fa ta zaɓa min. A inda ta barni anan na zauna har dare ban motsa ba dare da naga karnuka na zuwa wurin cin abinci na bar musu duk abinda ta bani don ba zan iya amfani dasu ba na koma wani gini da ba'a ƙarasa ba na zauna daga ranar na rasa bacci na Abeeyy daga na rufe idanu kalaman ta su ke farautar numfashina....A ranar Ammie ba rabuwa da ni kawai tayi ba ta kashe ruhi da zuciyata kisa mafi muni na yi kwana biyu ban iya cin komai ba sai ruwa kan wani almajiri ya ja ni muka fara sana'ar wanke gilasan mota Dukda ban taɓa mishi magana ba amma shi yana min surutu sossai, kayan aikin nashi ne idan ya gaji zai bani in yi ko kwanaki goma ba'a yi ba garin wanke gilasai mota ta kaɗe shi ya rasu, kayan aikin nashi na cigaba da amfani da su har Allah ya haɗa ni da Mammi.." Nan ya cigaba da bashi labarin komai da komai mai martaba banda hawaye babu abinda yake, a lokacin da ya zo rasuwar Mammi sai da hawaye ya ziraro mishi ya sa hannu ya ɗauke jijiyoyin kanshi duk sun tashi raɗa raɗa idanunshi sun yi ja sossai da sossai. Shiruuu ne ya ratsa parlorn fiye da mintuna biyar Abeey a hankali ya ce "Mahaifiyarka ta cuce ni ta ci amanata Sameer! Ban san me zan yi na huce wannan zafi da raɗaɗin da nake ji ba... Bata da uzurin bani na wannan laifi da ta aikata. Hakika na so Mammin ka tana raye in ganta ido da ido in yi mata tarin godiya marar adadi akan kaunar da ta nuna maka sai dai kash! Allah bai taɓa barin wani don wani yaji daaɗi ba idan ajali ya zo babu mai ƙara ko da second guda ne sai an tafi, a yanzu ma bata ɓaci ba za mu tabbatar mun yi tarin abubuwan alkhairi masu yawa da sunanta don ladar ya je mata a makwancinta. Allah ya musu rahama ita da mai gidanta ya sada su da annabin rahama" Ya amsa da ameen "Ɗauki ipad ɗin chan ka kira min Mahaifinta video call za mu yi magana" Ipad ɗin ya dauka ya saka numbern uncle Musa ya kira aka taki sa'a yana online ya ɗaga zaune yake da Uncle sanusi da Uncle Mansur suna tattaunawa ganin fuskar Rayyan ya sa suka yalwatu da fara'a ya shiga gaishe su yadda ya saba suka amsa kan ya mayar da fuskar kan fuskar Abeey ba tare da ya ce komai ba. "Assalamu Alaikum warahmatullah..." Amsawa suka yi suna ta kallonshi kan Uncle Mansur ya zare idanu "Laamiɗon Fombina mai girma Muhammadu Modibbo Aliyu.." Duk sai lokacin suka ɗago suka shiga gaishe shi da girmamawa don shima ba ƙarami bane idan bai girmi uncle Musa ba za su yi sa'anni. Sannan ko babu girman shekaru akwai na mulki da sarauta mai girma. "Na yi muku laifi ina Fatan za ku yi haƙuri ku yafe min kuma ku dubi uzurina, kaman yadda kuka sani sunana Muhammadu Modibbo Laamiɗon daular kudu maso arewacin Kasar nan, a cikin tarihina ina da ɗa namiji tilo da ya ɓace da kananun shekaru inda an yi neman duniya an rasa shi sai satuttuka da suka wuce Allah ya bayyana min shi. Wannan yaro ba kowa bane face ɗan ƴar wurin ku mai rasuwa wato Rayyan a chan anan kuma Muhammadu Sameer" "Allahu Akbar kabiran! Allah mai girma! Allah mai yadda ya so iko sai Allah ashe dama Rayyan ɗanka ne? Kai Alhamdulillah wannan abu na farin ciki ne Alhamdulillah ina ma Mamanshi na raye ta ga wannan rana..." Uncle Musa ke fada cikin tsananin farin ciki suka shiga taya su murnar saduwa da juna. Bayan gama barka da jaje Mai martaba ya ɗora "Laifin da na muku shine na sanar da ku a waya, shi Ciroman ya so ya je ne don martabarku ya shallake haka a gareshi amma ban ba da goyon bayan hakan a yanzu ba, zai iya zuwa ziyara ko wasu kananun al'amura da bai kamallah ba amma sai ya gama blending da dangi ina fata hakan bai ɓata muku ba, in shaa Allah zan yi tattaki na zo da kaina na kawo ku kuga inda yake" Uncle Musa ya ji daaɗin martaba da ƙimar da aka basu yace "Ba sai ka zo ba ranka ya dade da kanmu za mu zo har nan mu taya ku murna in shaa Allahu" "Sai abu na ƙarshe ban san ko za'a yi min wannan alfarma ma" "Alfarmar ka ya wuce ka roƙa mai martaba sai dai umurni" Uncle sanusi ya faɗa don basu taba zaton sarkin haka yake da saukin kai da iya mu'amala ba Dukda tarin dukiya da irin rigar mulkin da yake ciki hakan bai hana shi yi musu magana cikin girmamawa da fahimta ba. "Idan za ku taho ɗin ba matarshi kawai za ku taho da ita ba, za ku taho min da 'ya'yana Jannah Da Abeeha ita jannah za ta koma ne kawai saboda auren dake kanta Abeeha kuwa ta zama tawa aure ne zai fitar da ita daga wannan gida bi'izinillahi" Sun gamsu suka yi godiya don martabarsu ne Dukda suna da dukiyar da zasu iya rike Abeeha amma Mammi Rayyan ta barwa shi kuma duk inda Rayyan yake dole ta zauna dashi... Bayan sun ajiye kan sadarwan Mai martaba Laamiɗo ya dubi Ciroma "Alhamdulillah! Yanzu ka je kayi shirin juma'a idan an sauƙo akwai media team da suke son ganawa da rundunarku da kuka ceto su Aissatou to amma su sun tafi bayan na sallamesu don komawa ga iyalan su bayan sun bar nan shugabanku ya kira ni akan ba za su iya zama har Washegari ba dole na wakilta Galadima ya je ya min godiya ya kuma sallamesu kai za ka gabatar da shirin madadin ku gabaɗaya" Bai so ba amma ya ya iya dole ya amsa ya yi godiya ya miƙe ya fice. Yau suka yi finals jiya garin gigin baccinta an dauke musu wuta kuma ba'a yi rana ba don ruwa suka samu basu samu chargy a solar ba kan a kunna gen ta tafi fitsari ta jefar da wayanta a ruwa, ta ji haushi saboda bata da wayan kallonshi tunda ba ya kira yanzu, sossai take jin kewanshi kaman sun wani saba sukuku ta shigo parlorn abin da ya kamata tana murnar kamallah secondary da aka yi da kyar amma damuwar da zuciyarta ke ciki ya hana ta. A babban parlor ta samu Abeeha na kai da komo wa tamkar ruwan cikin kwano ta kasa zaune ta kasa tsaye ganin Afeefah yasa ta daka tsalle ta riƙo hannayenta "Afeefah mun warke... Innalillahi wainna ilaihi rajiun khaihhh farin ciki zai kashe ni...! Afeefah Albishirrinki.." Cike da zumuɗi take maganan har jikinta na rawa "Goro.." Ta faɗa cike da mamakin me ya saka Abeehar farin ciki haka "Afeefah kin zama Gimbiya matar yarima ko in ce Sarauniyar gobe matar Saraki... Ashe Saraki da Mammi ke kiran Ya Rayyan ba'a banza ba? Afeefah mijinki ashe ɗan babban sarki ne mai tarin daraja da tushe me kyakyawar asali? Ashe ya Rayyan jinin sarauta ne ke yawo cikin jikinshi? Kaii amma Allah ya isa wa mahaifin yarinyar nan da ya kalleshi yace kila ba tsatso mai kyau aka samo shi ba ya ci mutuncin sarauta.." Afeefah dai ta kafe a tsaye tana ta kallon Abeeha na zuba chan tace "Anya Adda Abeeha lafiyarka kuwa? Wani irin magana kike tayi ba kan gado...? Wani yaya Sarakin?" *Wayyo Hannun mar'atussaliha😩 🖤Gureenjoh🖤 HAIHUWA DA HANJI (A True life story) Fatima Muhammad Gurin (Gureenjoh) Wattpad-Gureenjo6763 Arewabooks-Gureenjoh ADABI WRITERS ASSOCIATION *FREE BOOK* *47* "Yaya Rayyan mijinki nake magana a kai girlll wlh da gaske nake miki yanzun nan Baba Musa ya ƙira ni yake cewa za mu shirya tafiya Fombina gobe sun sayi tickets already, ya ce mu shirya kaya kuma mu kintsa komai don za mu iya ɗan jimawa bamu zo kd ba." Bata san me ta ji ba a lokacin mamaki ko tsananin farin ciki, tayi matukar taya shi murnar reconsiling da iyayenshi don dole su ɗin su ne dolenshi ko ba jima ko ba dade, ashe yana da alaƙa da sarauta? Fuskarta cike da murmushi tace "Alhamdulillah Allah mun gode maka" Wani sashe na zuciyarta kuma tsoron tafiyar take don bata san me kuma zata tarar ba, hakika ta fi jin natsuwa da kwanciyar hankali a gidan na Mammi, sai ta fara tunanin idan basu karɓeta ba fa? Dama gashi ba sonta yake ba kila suna ce mishi ya rabu da ita zai rabu da ita a yadda ta san tsarin gidan sarauta. Abeeha ta wuce ta shige sashensu zuwa ɗakinta ta samu bakin gado ta zauna "Allah mai girma annabi mai dumbin daraja! Yanzu ni ce Afeefah ke da matsayin matar ɗan sarki mai daraja a wannan ƙasar? Anya? This is too good to be true... Hankali ba zai kama ba ni Afeefah dai ta Dutsen-wai annoba Mayya ajalin duk wanda ya raɓe ki!" Bata san adadin lokutan da ta dauka zaune a wurin ba har lokacin sanye da uniform don ba sallah take ba bare tayi tunanin azahar da aka idar a wasu masallatan, tana nan zaune sai ga Abeeha ta shigo da sauri bayanta jannah tana cewa "Zo ki ga wani abu Khaihh Ya Rayyan duniya ne! Sarakin Maammi ne a gasken gaske an tashi kaina!" **** Yana fita daga sashen Laamiɗo Saleem ya ƙira yana tafiya a hankali suna magana sun jima sossai suna wayan Saleem ya san komai a kanshi ya kuma taya shi murna kwarai shima kuma yana cikin masu tahowa gobe ɗin, idanun Rayyan ne suka sauƙa akan Fulani Adama dake tahowa hanyar sashen mai martaban, bai wuce ba sai ya tsaya yana cigaba da wayan idanunshi na a kanta yadda take tafiya cike da izza da takama bayi da kuyangi na zube mata ko kallo basu isheta ba ɗauke ido yayi ya cewa Saleem "Zan saka maka wani abu ka sallami duk ma'aikatan gidan ka kuma ba su haƙuri na barin aikin ba tare da an sanar da su da wuri ba, za'a basu abin da zai ishe su jarin wata sana'ar in shaa Allah. Please a rufe komai yadda ya kamata don zan dawo ba na zo kenan ba!" Kalamanshi na karshen karab a kunnenta, idanu ta zuba masa Dukda kaɗuwar da tayi na namijin da ta gani a gabanta ta wani sashen ta ɗan ji sanyin kalaman nashi har hakan bai ɓuya a kan fuskarta ba sai da tayi murmushi ya sake kawar da idanu a kanta yace "Na gode Saleem za mu yi magana please ka sanarws Sulaiman kafin na ƙira shi, Sai na ganku a gobe ɗin..." Yana sauƙe wayan ya kalleta "Barka da wannan lokaci Mama..!" Ya faɗa da ɗan murmushi mai dauke da dumbin ma'anoni. "Ashe rai kan ga rai Sameer? Ko da shi ke na zaci ka manta da mu gabaɗaya ai shiyasa ban ga ka kawo gaisuwa ba..." Har lokacin yana dan murmushi yace "Wani abin ake mantawa amma wani ya fi ƙarfin mantuwa Mama, zan zo in shaa Allahu ban gama warware gajiyar aiki bane. Na bar ki lafiya" Yana kai nan ya wuce ta Gaabɗo ya bishi da sauri. Da kallo ta bi bayanshi sama da mintuna biyu kan ta juya ta nufi sashen na mai martaba. **** Saleem na sauke waya ya kalli Mommy dake zaune cikin kujera a sabon gidansu da suka dawo komai na ciki sabo ne kuma a tsare gwanin kyau da ɗaukar ido yace "Mommy kin ji ikon Allah ko?" Duk su Sameera idanu suka mayar kanshi mommy tace "Me ya faru?" "Mommy ashe Rayyan jinin sarauta ne, mahaifinshi shine Laamiɗon Fombina." "Da gaske kake ko wasa?" Cike da dumbin mamaki mommyn ta jefa mishi tambayar "Wallahi da gaske mommy yanzu haka yana masarautar su ashe ƙanwar shi ce aka yi kidnapping suka je suka samu sa'ar tseratar dasu, gobe duk su Afeefah za su tafi chan nima yanzu zan sayi ticket" "ikon Allah ikon gaske, wato a wannan duniya ka kalli mutum ne kawai baka san waye shi ba, No wonder yake da ɗabi'ar sarautar... Ikon Allah wannan abin mamaki dayawa yake" Sadiqa tace "Oh wa zai tuna Afeefah za ta iya sa'ar zama matar irin wannan mutumi? Yanzu mu fa ko kallonshi sai da hanya...waye bai san irin tarin dukiyarsu, karfin mulkinsu da izzarsu ba!" Samha tace "Gaskiya tayi dace kam tsuntsu daga sama... Mun mata murna Allah ya cigaba da basu zaman lafiya haɗe da zuri'a dayyaba" Duk suka amsa da Ameen amma mamaki da tsoron Allah na sake rufe su rufff. Saleem ya miƙe ya fice daga gidan. **** Kitchen ya shiga kai tsaye bayan shigarshi sashen ya dafa indomie don babu abinda babu na girki cikin babban kitchen ɗin komai na zamani komai kuma fess kaman ka lashe don walwali, a plate ya juyo ya dawo parlor hannunshi ɗaya rike da ruwa yana gama ci ya mayar da kwanonin ya wuce ɗaki bai samu ya Kira Abeeha da ya ga missed call nata ba saboda lokacin masallaci dake kokarin ƙurewa ya sauya kaya zuwa wasu Fararen jumpha hadadden ɗinki 'yar ciki da babbar riga ya fita yayi kyau ainun daga ka ganshi zaka san yaro da kuɗi ne abokin tafiyar manyan, ga sarautar amma ya tafi da tsantsar wayewa, ilimi da sanin kan tsarin shiga. Hula da takalmin da ya saka duka farare fatarshi sai shining yake Dukda ma ya ɗan yi duhu kaɗan saboda zaman da suka yi daji amma fess yake ba ma zaka gane ba idan ba ka san shi ba, turare ya feshe jikinshi da su kala daban daban kan ya zari wayanshi ya fito tuni duk suka miƙe dogaran suka fara zabga mishi kirari ya ɗaga musu hannu don bai cika so ba yayi gaba suka rufa mishi baya har mota, Dukda masallacin ma a cikin masarautar yake sai dai akwai 'yar nisa don haka dole mota ya shiga suka yi har motoci uku da dogaran suka nufi masallaci. Mai martaba na shiga shima ya iso ya shiga nan aka fara huduba bayan an gama tsaf aka gabatar da sallah kaman yadda addini ya tanada aka yi adu'o'i kan aka shiga watsewa a hankali, daga nan fada suka nufa don sarki na son ganinshi yana isa gaban manya jagoran addini da al'ada na fulani wato Laamiɗo ya gabatar dashi a matsayin Ciroman Fombina kuma Yarima Fuunange na ƙasar Fombina (Yariman Matasa) a take aka mishi rawani fari ƙal mai kamshi wow ya fita kaman ka sace shi ciki, kasancewar wurin akwai yan jarida kala kala tuni ya fara zagaya duniya. Turaki ne ya karɓi abin magana ya gabatar da kanshi kan ya ce "Ciroma alhakina ne da in sanar maka aikin matsayinka, na san ka riga ka san Ciroma shine wanda aka ɗauka matsayin ɗan gado ko mai jiran gado. Yarima Fuunange wato Yariman Matasa kuwa mun bar maka goben matasan mu ne a hannunka, kai ne shugabansu wurin ganin sun cimma al'adar mu na fulani bisa kan daidai wato: • Koyon Pulaaku (hakuri, ladabi, kunya, jarumta). • Koyon sana'a ko aikin iyaye (kiwo, noma, ko fatauci). • Haskawa a cikin al'umma ta hanyar waka, rawa, da wasan al'adu da gargajiya. Muna yi maka Fatan alkhairi da Fatan Allah ya baka ikon sauke wannan nauyi da aka ɗora maka" Tuni sarkin busa ya fara busa algaita mai daaɗin sauraro dogarai suka shiga jefo kirari daban daban, ya miƙe tsaye ya isa gaban mahaifinshi yayi godiya ya juya aka yi mishi rakiya da wannan busa da sarewa "Taaakawarka lafiya ɗan sarki jikan sarki kuma uban sarkin gobe, kaaaareka Ciroman duk duniya Yariman Matasa gaba saalaamun baya salaaamun, maƙiyanka fadawarka ɗaawisu sarkin ado... Kyaun ɗa shi ne ya gaji mahaifi kaareka Ciroma" Abin da ake ta nanatawa kenan busa da sarewa na tashi har parlorn baƙin shi na sashenshi inda anan zai gana da 'yan jaridar da suke jiran shi kan aikinsu. Zama yayi ya ɗora kafa ɗaya kan ɗaya yana dan lumshe ido ya buɗe saboda gajiyar da yayi ga chan ƙasan ranshi wani abu na mintsininshi na kewar abin da zuciyarshi ke mararin ko da sauraron muryarta ne bai samu dama ba. "Ranka ya daɗe Dukda abin da ya ajiye mu anan daban sai dai za mu fara ne da taya ka murnan shigowa cikin ahalinka lafiya, shin me za ka iya cewa akan farin cikin da kake ciki a yanzu? Menene kuma ya zama babban mukamin bayyanarka a wannan lokaci?" Murya ya ɗan gyara bayan yayi sallama da Fatan alkhairi kan ya furta "Komai lokaci ne na yarda da wannan, sannan bafulatani yace Munyal deefan hayre, ko va'i fu jippan"(mai haƙuri kan dafa dutse kuma duk nisan jifa ƙasa zai dawo)" Amsar kenan da ya bayar, dan jaridar ya zaci zai kara wani abu amma sai ya ji shiru sai yace "Masha Allah, Toh bari mu koma abin da ya ajiye mu anan shin menene ya faru? Ta ya aka yi taron al'umma suna jiran ganin waennan miyagu sun kasance Fulani kaman yadda aka jima ana yi wa Fulani kuɗin goro sai kuma aka haihu a ragaya?" "Dama chan kulba ta jima tana ɓarna ana cewa jaɓa ce, bana manta ina da wani shugaba a baya da sanadiyar kudin goro da ya mana ban taɓa furta mishi ni bafulatani bane amma ya kafa min karar zuka ban ci mishi ba ban sha mishi ba, hakika wannan irin zato na duk bafulatani ɗan ta'adda ne ya jima yana ciwa dayawa tuwo a ƙwarya. Ba a tuna baya in ji masu iya magana wai gyartai ya ci sarauta, a lokacin da duniya ke kwance kabilu mabanbanta kan shiga rugagen Fulani ayi wasa tare, a ci abinci tare a sha kindirmo a dalilin haka har zumunci ya ƙullu sai auratayya ta shiga tsakani. Da tafiya tayi tafiya a sannu sannu aka fara kwacewa Fulani shanu da matayensu a rugage kafin komai ya ta'azzara da abin ya fara zuwa gidan gona da kauyuka sai aka yi musu kuɗin goro aka far musu da kisa na kan me uwa da wabi wanda kan iya ɗarsa ɗaukar fansa, dayawa daga cikin Fulanin da suke rayuwa a daji babu ilimin addini ba na zamani, malamai babu ruwansu da kai da'awa, gomanti babu ruwan ta da samar da ingantacciyar ruwa ko makarantun zamani, aka kwace sandunansu na kiwo aka damƙa musu makamai saboda wani ƙudiri kawai na samun duniya a ji daaɗin cin ta da tsinken sakace. A hankali ringingimu suka fara yawa ta yadda zaman lafiya yayi mana ƙaura hakan ya shafi har waenda basu ji ba basu gani ba, shi fa ɗan ta'adda bashi da ƙabila, yare, addini ko jinsi in dai mutum bai da imani ko wanene shi bahaushe, Fulani, kanuri, yoruba ko igbo zai iya kasancewa ɗan ta'adda hasali ma ku sani ba Fulani bane suka aikata mana wannan ta'asar idan ma su ne suka aikata wa wasu daga cikin mu a wannan karon ba su bane don ma turanci ne tsantsa a bakin waennan, makamai da abincin da suke ci be yi yanayi da na bafulatanin ruga ba sai na wayayyen mutum ɗan zamani amma kuma idan zasu yi hausa su kan yi da sigar harshen Fulani Lallai an jima ana ruwa ƙasa na shanyewa." Ɗan jaridar cike da gamsuwa yace "Barka da Yariman Matasa Ciroman Fombina, hakika gwalagwalan kalamanka sun fi yanayi da na hikima Allah ya sa mu gane. Toh wace hanya kake gani za'a bi wurin dakile wannan al'amari da ya ta'azzari al'umma yake kuma lalata musu Matasa?" "Hanyoyin masu sauƙi ne ga al'umma amma masu wuya ga gomnati don zai kawo musu cikas amma idan al'umma suka tashi suka yi aiki a tare za'a iya maganceta cikin sauƙi, hanyoyin za su iya haɗa wa da • Karfafa tsaro da sa ido a kan dazuka da hanyoyi. • Ƙara horo da kayan aiki ga jami'an tsaro. • Bincike da hukunta masu laifi cikin hanzari. • Ƙarfafa al'umma da aikin yi ga matasa. • Ƙarfafa haɗin kai tsakanin al'umma da hukumomi - wato tsaro na gari. • Ƙin biyan kudin fansa - domin rage ribar garkuwa" Yana maganan ne yana ƙirgasu da yatsun shi cikin aji da iya magana. Kanshi duk ya ishe shi da ciwo da kyar ya gama sallama da mutane yayi la'asar ya shiga ya kwanta yana lumshe idanunshi da suke mishi nauyi ainun duk yadda ya washi baccin yamma bai san ya ɗauke shi ba don ya sha magani ga gajiya da ya tarar mishi. *** Idanu kawai Afeefah ke Binshi dashi tun sanar da dawowanshi hasko shi da aka yi ana mishi sarautar Yariman Matasa da ma hirar da aka yin don live ne a manyan jaridu har international, Fatan alkhairi da ake Binshi da shi da yabon da yake sha duk suna kallo a ipad ɗin Abeehar, ita dai ta rasa me ke damunta ma hawaye kawai ta fara tsabar feelings ɗin sun zo mata daban daban, ya mata kyau ba ƙarami ba yadda kuma ya mata ta san yayiwa yanmata dayawa, kishi na taso mata sai kuma ta shiga damuwar anya ma a mace ya dauƙeta? Don ko ta wani ɓangare tana ganin ita ɗin ba tsararshi ba ce, tun daga tsatso, asali, ilimi, dukiya da kuma mulki ba ta inda tayi matching da shi kenan 'yan uwanshi za su iya ware ta yadda take jin labarin gidan sarauta? Meyasa be neme ta ba? Sukuku haka su Abeeha suka taya ta haɗa kayanta akwati biyu suna ta surutu bata ce musu komai don faɗuwar gaban da take fama dashi kaɗai ya ishe ta, ko da suka bar ɗakin kifewa kawai tayi ta saki kukan da bata san na menene ba, ko abinci bata ci ba tayi kuka ta koshi har bacci ya ɗauketa a haka wuraren bakwai na dare. **** Shafa fuskar ipad ɗin take da ake nuno hiran tana kuka, tana ganin yadda yaronta ya girma ya zama mutum, tana ganin tarin baiwa da nasaba da Allah yayi mishi tana jin guilt na tauye mishi wannan hakki tun daga yaranta, tana tuna yadda ta zame kafafunta daga cikin hannunshi tana tafiya ta barshi a bakon wurin da bai san kowa ba.... Bata ga laifinshi ba don bai zo inda take ba itama kunyar fuskantar shi take ji kaman ta nitse. Turo kofan aka yi aka shigo, ta ɗaga kai ta kalli Aisha, Matashiyar kyakyawar yarinyar da ke tsananin kama da Rayyan ɗin ta iso gangarta "Ammi Meyasa kike son sakawa kanki damuwa har haka? Baya nan kullum kuka da tunani ba ki samu cikakken farin ciki ba ya dawo ma baki huta ba? Gashi shi ko ya damu dake tunda bai tako kafarsa ya zo inda kike ba?" "Aisha bashi da laifi don bai zo ba, baki san me na aikata mishi bane" "ko me kika aikata mishi uwa fa uwa ce Ammi don Allah tunda ya bayyana cikin koshin lafiya yana ci yana sha kuma babu abinda ke damunshi ki bar wannan kuka haka ki nemi natsuwar ki" Da lallami tayi maganan, Ammie tayi murmushi mai ciwo sati uku kenan ko kallonta mai martaba bai sake yi ba bare har yayi magana da ita, ta san tayi kuskure amma su saurare ta kan su yanke kowani irin hukunci, tana kuma ganin Aishan bata san zafin dake cikin Abandoning bane ta tashi gaban iyayenta da gatanta shiyasa take wannan magana amma ita ta san dole sai an dauki lokaci Sameer zai sauƙo. Karfe shidda ya tashi ya watsa ruwa yayi sallah kan ya kira Abeeha ta ɗauka suka gaisa kan yace "Me kaman Muryar jannah nake ji?" "Eh Yaya ta zo ne da shirin tafiya akan gobe kawai sai mu wuce airport daga nan" "Me zai faru idan goben kuka haɗu airport da ita? Mijin yarinyar nan na sakacin barin matarshi sakaka tana yadda take so fa... Ina Afeefahh?" Miƙewa tayi "Bari na kai mata tana ɓangarenku" "Wayanta fa me ya same shi?" "Ruwa ne ya shiga sai ya ɗauke Yaya" Bai ce komai ba chan kuma ya fara ja mata kunne akan su tabbatar basu bar komai da zai iya lalacewa a gidan ba tana amsawa har ta tura ɗakin Afeefah da sallama. "Yaya ta yi bacci fa in tashe ta?" Ya ɗan yi shiru yana jin ba daaɗi kaman ya ce eh sai kuma yace "Kyaleta..amma sallah fa?" Sai tayi shiru ya fahimta don haka yace "Shikenan! Da safe za mu yi magana" Ta mishi sallama ya katse wayan ita kuma ta fice daga dakin. 🖤Gureenjoh🖤 HAIHUWA DA HANJI (A True life story) Fatima Muhammad Gurin (Gureenjoh) Wattpad-Gureenjo6763 Arewabooks-Gureenjoh ADABI WRITERS ASSOCIATION *FREE BOOK* *48* Washegari saboda tarin gajiyar da ke jikinshi bai iya ya farka ba tun bayan Sallar asuba sai wuraren karfe sha ɗaya, ko da ya kalli time ya san any moment from then sun kusa isa already Mai martaba ya tanadar da duk motocin da za su ɗauko su daga airport da ma masauki har da abin da zasu ci kan ya zauna da su gabaɗaya yadda ya shirya. Wannan dalili ya sa kawai ya shiga wanka a natse yake komai cikin sarauta da ya bi jiki, ya fito ya shirya cikin manyan kaya mint green ne yadin mai ɗan duhu ya mishi kyau ainun ya feshe jikinshi da turaruka kan ya fito parlor sai karab idanunshi suka sauƙa akan kuyangi har biyar da suke zaune daga chan kusurwan parlorn bai tanka su ba ya shiga kitchen ya haɗa tea ya fito ya zauna tare da crossing legs nan suka fara kwasar gaisuwa kai ya gyaɗa kan ya yi kiran Gaabɗo yana cigaba da sipping tea din yana karkaɗa ƙafafu. "Wa ya aiko su?" "Uwargida Fulani Adama ce ranka ya dade ya baka yawan rai" Ya amsa Bai ɗago ba idanunshi na kan waya yace "Duk su bani wuri ba na son ganinsu ka kuma tabbatar basu sake shigowa sashen nan ba" Da sauri ya amsa ya juya ya kallesu tuni suka miƙe suka tafi ɗin. Ba'a jima da tafiyan su ba sai ga kira daga mai martaba dole ya miƙe ya nufi sashenshi, a zaune ya same shi shima ya samu wuri ya zauna ya kwashi gaisuwa "Mamanka ta kawo min ƙararka, Meyasa ka kori kuyangin da aka tura sashenku? Ka dai san ko kai baka buƙata matarka tana buƙatarsu saboda hidima" "Basu yi min bane ranka ya daɗe" Murmushi mai martaba yayi "Toh shikenan zan yi magana da jakadiya sai ta kawo maka wasu" Shi dai idan ba don mai martaban ba da ba wata da za'a tura mishi shashe amma bai ce komai ba. "Baƙinmu za su iya sauka cikin kowani lokaci motoci na nan suna jiransu a Airport da Wambai da shi na wakilta ya tarbe su saboda muhimmancinsu" Ko kan yayi magana aka fara sanarwar Shigowar Mahaifiyarshi Dukda yadda gabanshi ya faɗi zuciyarshi ya chanza bugu hakan bai sa ya ɗago kai ba kanshi na kasa har ta samu wuri ta zauna ta mayar da kanta ƙasa a hankali hawayenta ke diga bisa kan kyakyawar shimfidar parlorn. Shiru wurin ya ɗauka kan a hankali Rayyan yace "Barka da safiya ranki ya dade" Bai jira amsarta ba ya miƙe zai fice tayi saurin ɗago kai tace "Sameer...!" Chak ya tsaya yana jin sunan har cikin ranshi sai dai yana tuna ranar da ta mishi umarnin cewa ya manta da ya taɓa amsa wannan sunan, ya manta ya taɓa sanin su a rayuwarshi. "Kaico na! Kaicon uwar da ɗan ta ba zai iya ɗaga idanu ya kalleta ba saboda wani tabo da ta samar masa mai wuyar warkewa, Don girman Allah ka dawo ka zauna ka saurare ni, Mai martaba ka yi min alfarmar tsayuwa ka ji uzuri na idan kai kana fushi shi yana fushi wani hali kuke so in shiga? Wani hali kuke so ku riske ni a ciki kan tausayina ya darsu a ranku ku ji cewa za ku iya min uzuri? Ni fa uwa ce ni kaɗai na san irin zafin ɗaukar ciki, rainonsa zuwa haihuwarsa da gayya ba zan salwantar da rayuwarka ba Sameer, da gayya ba zan ƙuntaci kaina tsawon shekarun nan ina kuka da hana kaina bacci wurin roƙon ubangiji ya baka ingantacciyar rayuwa da farin ciki ba... Don Allah ku saurareni ko da sau ɗaya ne" Tausayinta ne ya rufe mai martaba Dukda haushin ta da har yanzu yake cike a cikin zuciyarshi, wlh in bai ce har tunanin sakinta yayi ba yayi ƙarya kasancewarta macen da ya fara so kuma har abada yake jin sonta daban cikin matanshi bai sa yaji cewa zai iya yafe mata abinda tayi mishi ba amma a yanzu tausayinta ne ya fara rinjagayar fushin, kallon Rayyan da bai motsa ba bai kuma ya dawo ya zauna ba yayi yace "Ciroma samu wuri ka zauna" A dole ya zauna ko sau daya bai kalleta ba don idan ya kalleta zai iya jin zafi da raɗaɗin shi ya ƙaru kaman yanzu yake tuna yadda ta jefar dashi aka ce zuciyar yaro babu mantuwa a daidai lokacin da yake jin daaɗin rayuwarshi yake kuma da gatan shi ta zabi mayar dashi marar galihu har ma ana kallon idanunshi ana mishi zancen kila shi ɗin shege ne marar uba! Idanu ya runtse kukanta har ranshi yake ji amma baya jin kukan a matsayin uzuri. "Ban san ta ina zan fara ba amma na san duk kun san cewa a wannan gida na sarauta aka haife ni amma ban tashi nan ba kasancewar mahaifiyata ta rasu ina da kananun shekaru, na koma wurin dangin mahaifiyata da zama ta yadda duk wani tuggu, makirci ko fuska biyu na gidan sarauta ban sanshi ba, i was a care free person with a pure soul ina rayuwa kaman kowacce mace ba tare da na san akwai alkawarin auren sarkin gobe a kaina ba kasancewar mahaifina Galadima kuma har yanzu gidanmu ke sarautar Galadima, ina da shekaru goma sha huɗu Yaya Maudo ya turo kuyangi na musamman don su fara horar dani zaman cikin masarauta da ma abin da ya kunsa Dukda a lokacin kana da uwargida wacce itama duk jini ɗaya ne tunda daga Makama har Madaki sarautar gidansu ne kuma kun fi kusa kusa sossai don First cousins kuke har gobe idan babu jininka wani daga gidansu yana da damar zama Sarki. Kana kuma da Fulani Aminatou da aka baka ita daga masarautar Kamaru Dukda Na samu maganganu masu yawa akan masarautar na shigo ne a mace ta uku da shekaru sha shida kachal, kai shaida ne irin wahalar da na sha kafin nayi blending da rayuwar cikinta ban shekara biyu ba ka cike mata huɗu, dukkanmu daga kan Fulani Adama har Fulani Salimah babu wanda ya taɓa ko da ɓatan wata ne, dayawa sun fi damuwa da ita kasancewar ta fi mu jimawa tsawon shekaru kusan goma kuna tare, kwatsam na samu juna biyu an yi farin ciki kwarai kuma babu wanda bai sani ba ana kuma tattalin wannan ciki watanni biyu zuwa uku nayi mummunan mafarki ko da na tashi ciki ya bare duk mun yi bakin ciki amma muka sallamar Allah ne ke bayarwa kuma shi ya karba kayansa abin mamaki sai da na jera ɓari biyar a ƙasa da shekaru biyu, abin ya dame mu duka neman taimako da adu'o'i babu abin da bama yi har na sake samun wani cikin wanda kai ka hana mu fitar da zancen na tafi Mambila ban dawo ba sai da jaririna ɗan watanni har uku kowa yayi mamaki Dukda an zargi hakan don jimawa ta kuma an yi ta kananun maganganu ban damu ba don zuciya ɗaya na ɗauki kowa, abin bakin ciki yaron nan Aliyu na watanni biyar ya ce ga garin ku... Babu wanda ya san halin da nayi going through sama da kai mai martaba Dukda dukkanmu mun san ba haka kawai bane amma muka bar wa Allah kwatsam cikin Sameer ya bayyana wanda daga ni har kai bamu san da zaman cikin ba ma sai da yayi watanni kusan biyar. Babu irin wahalan da ban sha ba, babu irin ciwon da ban yi ba kaman ba zan rayu ba kaman zan rayu har Allah ya kawo min shi duniya, mun yi Adu'a kuma mun sa idanu da tsaro sossai kasancewar ranar da na haife shi kwana BOƊEJO tayi kukan murna Ganguna suka yini dokawa na maraba da sarkin gobe, Dukda hakan sau uku cikin shekaru biyu na Sameer ana poisoning ɗin shi da fargaba nake kwana nake tashi, kullum damuwata kar a samu nasara a kanshi mai martaba na rokeka sau ba adadi mu nesanta shi da masarautsr nan don ba zan juri rasa shi ba amma haƙuri da Adu'a shi kace mu cigaba da yi ba zaka iya nesanta da shi ba, kowa ya san Sameer ya taso ne kaifi ɗaya ga zuciya da jarumta, tun yana ƙarami ya san menene sarauta kuma ya san makiya da masoya Dukda haka bai tsira ba yana da shekaru huɗu ya ci poison da ya kwashi wattani tara bai san wanene a kanshi ba har mun fidda tsammani Allah ya sauko mishi da waraka ya farka, tsakani da Allah tun daga sannan na saka a raina cewa zan nemi hanyar bullewa don samun ya tsira da rayuwarshi, a haka na yanke kaishi ƙasar Hausawa na san namiji ne zai iya rayuwa kuma zan dawo in ta mishi Adu'a har karshen numfashi na. Wannan decision da na yanke daga ni sai Drivern da ya kaini wanda kusan amintaccen gidan mu ne da kuma kuyangata Kande da na san har abada ba zasu taba faɗa ba idan ba ni ce na faɗa ba, saboda in tseratar da rayuwarshi ya sa...." Katse ta yayi yana jin gabaɗaya mood dinshi na sake sauyawa zuciyarshi kaman akan wuta "Hakan ya sa kika yi mai gabaɗaya da rayuwata wai HAIHUWA DA HANJI ko? Kika kashe ni da raina Ammie... Har yau ina tambayar kaina me nayi da na chanchanci hakan ashe wannan ne dalilin? Idan ba don mutanen kirkin da na haɗu dasu waenda suka zama ba ni da tamkarsu a sanadiyarki ba zan iya cewa gwara na mutu da irin rayuwa cikin tsananin duhu da na yi a baya don bashi da maraba da rayuwa cikin ƙabari, Mahaifina da irin darajar shi da ƙimarshi an kalleni an ce min shege marar tsatso sau babu adadi wasu in ji wasu ban ji ba babu wanda ya fi tsaya min sai da aka hana ni aure saboda wannan dalili, kullum ina wurin likita ban taɓa bacci lafiya na tashi lafiya ba shine rayuwar da kike tunani ya inganta mini?" Hawayen da ya tarar mishi a idanu ya mayar ya miƙe kawai ya fice daga sashen, Ammie dake kuka sossai sai ji tayi mai martaba ya dafa kafaɗunta ya ɗaga ta sama sai kawai ta rungumeshi tana ci gaba da kuka mai tsuma rai. "Haƙiƙa kin yi kuskure amma har da laifina ciki, na sani ina da tarin makiya na ciki da waje, na san irin ciwon da kike ji a duk sadda kika rasa cikin ki na kuma san me kika yi facing a rasuwar yar ki ta fari Dukda mace ce, duk jinyar da Sameer yayi tare muka yi kuka amma ban yi tunanin nesanta ni dashi bane ba saboda bana son ya tashi a rago, na so ya san idan ya rayun ma cikin wuya da tsanani abinda yake gabanshi zai fi hakan, na so ya goge ne barazana ya zame mishi tamkar kuda da zai iya bugewa da tafin hannunshi ta inda na so kaina kenan na mance raɗaɗin da uwa za ta iya ji a sadda aka cutar mata da rayuwar da, amma Faɗimatu da sai ki tuna da idan rayuwarshi ya lalace fa? A wanchan wurin da kika ajiye shi zai iya zama ɗan daba, ko ya zama dan ta'adda ko dai ya faɗa wani mawuyacin halin da zai karar da rayuwarshi cikin mugun yanayi wanda duk alhakin zai iya zama a kanki ne!" "Sai da na bar wurin na fara wannan tunani mai martaba, haƙiƙa na yi ragon azanci wlh nayi nadama daga lokacin bayan kwana biyu da dawowar mu bana iya ko runtsawa gashi kana cikin halin ciwo da damuwa na tura driver sai dai ya dawo ya ce min bai same shi ba duk inda ya duba bai ganshi ba, daga ranar Adu'ata ta koma a kanshi na roki Allah kar ya bar min shi rayuwarshi ta tabarɓare na roki Allah da yakinin zai dubi zuciyata ya raya min shi har ma na samu cikin Aisha ban yi wani farin ciki ba, itama babu wanda ya san cikinta don kowa ya san ina jinya bana zuwa ko ina bana rabo da hijabi da chasbaha sai haihuwarta aka ji, nayi hamdala ganinta mace barazanar ta kuma ya zo min da sauƙi. Don Allah ka gafarceni ranka ya dade! Na tuba" Ya ja ta suka zauna ya riƙe hannunta. "Na yafe miki Faɗimatu na yafe wlh, wannan damuwa da kukan duk ya dameni ya hanani sukuni..." Yayi maganan yana share mata hawayen fuskanta, numfashi mai nauyi ta sauƙe. "Saura Sameer...!" Ta faɗa da wani yanayi. "kar ki damu zai sauƙo ne a hankali, don ma rayuwarshi bata lalace ba Alhamdulillah" "Ya baka labari?" Kai mai martaba ya gyaɗa nan ya shiga bata labarin abin da ya faru kabb yadda Rayyan ya bashi labari, tayi kuka sossai ta yi wa Mammi Adu'o'in da bata san iyaka ba, taji kaunar jannah da Abeeha tun kafin ta gansu taji cewa sun samu uwa har sai itama kasa ya rufe mata idanu in shaa Allahu yadda bata bar yaronta yayi maraicin uwa ba suma ba zasu yi ba. Ta roki mai martaba da ya bata riƙon Abeeha har tayi aure ya ce "wannan na ga yaron ki ne Fulani..! A yanzu kam bana tunanin zai amince bamu san gaba ba" Mai martaba ya ce "Amma ya kike tunani batun Zara'u kuwa? Kin san a yanzu da ya bayyana za'a saka mana ido ne a jira a ga me za mu ce tunda yarinya dai ta riga ta isa aure, kina ganin zai karbi auren?" "Ranka ya daɗe kai ka karance shi tun daga dawowarshi zuwa yanzu na dai san shi tun yana ƙarami da kafiya da taurin kai ban san ko ya chanza a hakan ba amma zan roki wani alfarma, ko da ya amince Don Allah batun jiyan matarshi da ka bani labari a barshi a rufe kaman yadda shima ya roke ka, mu ne kadai ke da alhakin sani a yanzu labarin na fita babu kananun maganganu da ba zaka ji ba, hakan zai iya zame mata barazana a zamanta cikin masarautar nan" Ya gamsu kuwa, su basu wani damu da jiyanta ba don sun yarda Mammi bata mishi zaɓen tumun dare ba kuma tunda ta gamsu da ita suma sun gamsu. Miƙewa Ammie tayi "Zan je na zaɓi kuyangin da zan tura musu da kaina, kuma zan tabbatar da cewa ba'a samu kuskure a hakan ba" Ya gyaɗa kai "Ki kwantar da hankalinki da fushin shi zai sauƙo with time musamman idan macen kirki yake dashi na tabbatar ba zata barshi ya cigaba da fushi dake ba nima kuma ba zan barshi haka ba" Tayi murmushi ta gyaɗa kai kan ta fice. Ta isa sashen kuyangi da kanta ta nemi kande ta nuna mata jikokinta ta zaɓi guda biyu da kuma ɗiyar wata Kuyangarta sa'ade ta tura su sashen Afeefah da sunan sune nata amintattun kuma ta tabbatar ba zasu cutar dasu ba, bata ma isa sashen ta ba ta samu labarin isowar baƙin masu muhimmanci. Ko da isowarsu Rayyan na tsaye a harabar masaukinsu inda ya tabbatar da komai ya tafi yadda ya kamata kuma masauki ne mai kama da apartment da babu wanda zai takura wani komai da komai akwai intact, hannayenshi harɗe a kirjinshi ya zubawa motocin idanu kawai yana so yayi tozali da ita ne ko zai samu sassauci, yadda yaji kewanta musamman a yau da ya san tana zuwa gareshi Allah ne kadai ya sani, kaman kuwa ta sani ita ta fara buɗe side ɗin da ke fuskantarshi ta sanyo kafa waje ta sauƙo, lumshe idanu yayi yana jin wani chill abu na ratsa shi daga inda yake tsayen, sanye take da wani 2 in 1 Abaya fari da ja da ya mugun amsarta. Gyalen mai bakin lace ne sai ta kawo lace ɗin Goshi kan ta zagaye sauran ya bar dankunnayenta Red colour fashion waje amma wuyanta ruff yake a rufe, hannunta jan jaka haka takalmin kafarta ma Red ne sossai ya shagala da kallonta sam bata lura dashi ba, ta riƙe kofan Jannah ta sauƙo tana tsokanarta akan ta rufa mata asiri kar a ga Gimbiya na buɗe mata kofa a zane ta ita kuma tana dariya tayi mishi kyau kwarai zuciyarshi sai motsi yake, da kyar ya iya kawar da kanshi ya mayar kan su Uncle Musa kan ya nufe so ba tare da ya bari ya sake kallonta ba don urge na jin ta jikinshi yaji yana ji kallon kawai ya mishi kaɗan, yana so yaji ni'imtaccen kamshinta a hancinshi, yana so yaga tana kallonshi da wannan tsoron a idanunta mai maiƙo idan ta tara hawaye, yana so yaji tana mishi magana a karye cikin tsoro da ya zama Shagwaɓa ko jan hankali a wurinshi amma duk ya bar wa anjima. Fuska a sake ya tarbe su, ita kuma sai da ya isa ya ɗan yi hugging Saleem kan ta yi noticing ɗin shi gabanta na ta dukan tara tara don tunda suka shigo gate ɗin masarautar ta rasa natsuwa, kanta har lokacin ya kasa dauka da ita ce matar magajin wannan masarauta mai girman gaske da ƙawa, mai tarin kuyangi, dogarai, bayi da hadimai. Mai dumbin tarihi motocin da aka dauko su ma kawai abin kallo ne sai dai ta ji jikinta ya sake sanyi ƙalau ganin ko kallon inda take bai yi ba. Gaabɗo ya kalla da sauri ya zube ƙasa "Allah ya baka yawan rai!" "Yi wa Uwar ɗakin ka iso zuwa sashenta" Yayi maganan yana dan kallonta sai suka haɗa idanu, kanta ta mayar ƙasa Gaabɗo ya matso ya zube gabanta don kallon da ya mata ya faɗa mishi ne wacece a cikinsu. "Lale Maraba da Uwar ɗakina Zinariyar masarauta mai daraja fiye da tagulla.. Maraba da hasken Masarauta mai haske tamkar farin wata... Sannu da isowa Gimbiyarmu Gatan Fada! Gimbiya mai rairayi cikin gaskiya...maƙi gani sai dai ya kau da idonsa hasken rana kike hannu baya karewa.. Allah ya ja da zamanin hasken zuciyar Ciroman duk duniya!" Duk sai ta rikice ta rasa ma me zata ce ta gigice ta kamo hannun Abeeha ta riƙe. "Barkanka dai!" Ta faɗa cikin rawar murya, Abeeha da Jannah sai dariya suke danne wa don tuni Rayyan ya jagoranci su Uncle sun shige ciki, yadda Afeefar duk tayi wuri wuri ne na rashin sabo ya saka su dariya shi dai cikin ladabi yayi gaba suka bi shi wasu dogaran suka ɗibo kayakinsu har zuwa sashenta. Kuyangin na zaune sai ga su duk zubewa suka yi suka fara miko gaisuwa ita Afeefah kuka ne kaɗai ya rage bata yi ba, Jannah ce tace "Wacece shugaba a cikin ku?" Suka nuna sa'ade "Nuna mana ɗakin uwar ɗakin naku tana so ta huta" "An gama ranki shi dade" Ta miƙe don da suka zo suka sanar da mahaifiyar Ciroma ce ta turo su Gaabɗo bai hana su ba kuma shi ya nuna musu ɗakunan masu Ɓangaren ɗayan suka kaita yayinda Abeeha da Jannah suka shiga daya don su yi wanka su dan huta. 🖤Gureenjoh🖤 HAIHUWA DA HANJI (A True life story) Fatima Muhammad Gurin (Gureenjoh) Wattpad-Gureenjo6763 Arewabooks-Gureenjoh ADABI WRITERS ASSOCIATION *FREE BOOK* *49* Bayan sun yi wanka suka fito parlorn, sun samu an jere musu abinci gashi nan kala kala suka zauna Afeefah na shirin serving ɗinsu ɗayar hadimar tayi saurin karɓa "Ranki ya dade duk wannan ba aikin ki bane" Shiru tayi tana kallon ikon Allah har ta gama serving ta koma chan gefe ta zauna. "Ni kam ina ganin ikon Allah" Sai lokacin ta tanka, Jannah tace "Ina baki labari kina ganin wasa nake yarinya, kin san ina karanta royal stories sossai wannan kadan kika gani" Abeeha tace "Ni fa in na samu irin gidan nan miƙe kafa zan ko wanka sai an min" Jannah ta maka mata Harara "Daaɗi na dake ragwantaka, kar ki sa in miki adu'ar aure inda za ki ɗora tukunya lamba goma" "Allah ya kiyaye ya kyauta wlh" Ita dai Afeefah dariya take musu chan tace "Ni dai kin san Allah duk waennan abubuwan basa burgeni, ni fa na fi so in yi rayuwata ba takura amma yanzu duk jina nake wani iri wlh" "za ma ki saba ne yarinya" Suna yar hirar su har suka gama suka dawo cikin parlor. "amma fa sashen nan naku wlh ya haɗu ƙarshe, ni kayakin nan ma na kasa tantance irin masifar tsadarsu ji kujera kaman bread tsabar taushi" Abeeha tayi maganan Afeefah tace "Kema kenan da kuka saba yawace yawace har kasashe ni ko da na shiga bayi sai da nayi kauyanci, wai ni Afeefah ce cikin masarauta har wani zube min ake a ƙasa abin nan ya kasa fita a raina" Jannah zata yi magana sai suka ji sallama. Dukkansu kofan suka mayar da hankali wata doguwar matsakaiciyar macece mai cike da kamala ta shigo sanye da rantsatsen alkhyabba fari tass daga ka ganta ka ga mulki fuskarta dauke da fara'a bayanta wasu 'yan mata biyu ne sanye da dogayen riguna suma kyakyawa don duk ruwan Fulani garesu. Kallo daya suka yi mata suka hangi kamanninta da Aliyu kan ma suyi magana kuyangin ta sun zube suna kirarin da ya sa suka fahimci wacece Dukda Sameer suka ji ake kira. Dukkansu suka yi yunkurin kaiwa kasa don gaisheta tayi saurin rike Abeeha da Afeefah ta ɗago su kan ta ɗago jannah duk ta rungumesu "Barkanku da zuwa 'ya'yana, Maraba lale da isowa masarautar Fombina" "Mun gode mama" Suka fada duka da murmushi a sadda ta sake su suka zauna tana rike da hannun Afeefah Dukda bata ma san wacece wace ba a cikinsu amma dai duk sun kwanta mata ganinsu hakan "Sannunku da zuwa" Aisha ta faɗa suka amsa da godiya. Zarah tace "Sannunku dai" Itama suka amsa. "Ni sunana Ammi ku daina cewa Mama akwai mamar taku Fulani Adama za ku je ku kai mata gaisuwa anjima, wannan ita ce Aishatu ƙanwar Sameer Yayanku su biyu Allah ya bani kan ɓacewarshi sai wannan ɗiyar wurin Makama cousins suke da su Sameer ko in ce Rayyan yadda kuka saba faɗa. Ina fata za ku dauke ni matsayin Uwa da kuka yi rashi gabaɗaya. Allah ya gafartawa Mammi ya kai haske makwancinta" Suka amsa da Ameen kan jannah tace "Ni ce Jannah, wannan kuma Abeeha ita ce kanwata Ga Afeefah ita ce matar Ya Rayyan" Ammi tayi murmushi tana kallonta "Masha Allah, Allah ya cigaba da baku zaman lafiya ya kawo zuri'a masu albarka" kunya ya hana Afeefah amsawa "Da ma na kasa haƙuri ne nace dai bara na zo na ganku, Abeeha duk abin da kuke so ko ya shige muku duhu ku kama sa'ade za ta kawo ku har inda nake ku tambayeni kun ji? Ke kam ma sashe na zaki dawo ba da jimawa ba" Suka yi murmushi ta dubi su Aishatu "Sai ku zauna nan duk abinda basu fahimta ba za ku iya fahimtar da su da kuma bayani akan family Dukda sai a hankali za su san kowa" Suka amsa kan ta miƙe ta fice suna mata sai anjima. Yadda su Aishatu suka kame haka dukkansu suka kame sai hirar ya koma tsakanin junansu kawai ita jannah ma waya take da mijinta yayinda Abeeha ke hira da Afeefah suna yar dariya, kaman daga sama sai ga shi ya shigo. Ko Aisha yau ne suka fara ganin juna dashi face to face, zama yayi a one seater ya kame yana kallonsu daya bayan ɗaya, jannah ta fara gaishe shi ya amsa ta mishi murnan dawowa cikin family Abeeha ma ta gaishe shi. Zarah ce ta gaishe shi ya kalleta yana son tuna sunan "Aammm.." "Zarah" "Oh Yeah lafiya ƙalau" Ya kalli Aisha da ta gaishe shi last itama ya amsa, Afeefah ce ta gaishe shi ya ɗan yi shiru kan ya kalleta sai ya miƙe ya nufi ɗakinshi. Abeeha ta miƙa hannu ta mistineta, kallon jannah tayi sai jannah ta harareta dole ta miƙe don sun cika ta da lectures kaman me akan Rayyan tun fitansu gida har hawansu jirgi zuwa sauƙansu magana ɗaya ake babu abinda basu gaya mata ba akan gidan sarauta sai ta tashi ta kama mijinta a hannu in ba haka ba ta ji a salansa. Ruwa ta haɗa a tray da cup mai tsananin kyau ta ɗauka ta nufi ɗakinshi, yana zaune bakin gado dafe da kanshi dake ɗan sarawa ya ji sallamar ta, bai ɗauka za ta shigo ba sai kuma ya ganta unexpected idanunshi masu shiga jikinta ya kafe ta da su yana yawo lungu da saƙo na jikin nata, tana sanye da doguwar riga peach mai roba ya fitar da duk wani shape ɗinta ta ɗaura dankwalin sai ta sako jelar guda ɗaya ya sauka har kan kirjinta tayi kyau sossai barin ma lips ɗinta dake shining na lip gloss. Ruwan ta zo ta ajiye mishi tana ɗan ɓata fuska, fuskar yake ta bi da kallo bayan ta ajiye ta juya zata tafi karab ya riƙo hannunta ya ɗan ja ta tayi baya baya ta zauna bakin gadon gefenshi har suna gogan juna ya juyo ya kalleta ba tare da ya saki hannun ba. "Haɗe ran nan fa?" Yayi magana yana dan ɗage gira guda alamun tambaya, lumshe ido tayi don maganan ta ji shi ne har cikin zuciyarta. Bata san ta narke ba tayi shiru bata ce komai ba. Kuma sai bai ji haushi ba sai ma kyau da ta mishi yadda take yi da fuskan itama kuma ta ji daaɗi da bai mata ihu ba sai ma Ruwan da ya ɗauka ya sha kaɗan ya ajiye yana dafe Goshi da hannunshi ɗaya har lokacin ɗayan na cikin hannunta yana dan motsawa a hankali. "Ba ka da lafiya ne?" Ya ji tambayar nata sai ya buɗe idanunshi da suka ɗan sauya ya kalleta ya ɗaga mata gira ɗaya "Sorry" "Kin san Meyasa ban amsa gaisuwarki ba?" Ta girgiza kai ashe ya san laifin da ya sakata fushin ma. "Saboda ba haka ake gaisar da miji ba madam..." Kan tayi wani magana ya ja hannun nata sai jinta tayi kirjinshi ya rungumeta ta runtse ido tana jin zuciyarta na chanza bugu, a hankali ta sa hannunta ta riƙe shi yayi baya baya ya jingina da jikin gadon ya ɗan lumshe ido. "Ya kike?" Taji maganan daga sama, ita dai ta rasa gane kanshi so yake sai ya zautata ko menene? "Lafiya ƙalau, ina taya ka murnan reunion ɗinka da family... Na kuma ga naɗi Allah ya taya riƙo" Ya yi murmushi kaɗan kan yace "Ameen, thanks" Suka yi shiru, ƙoƙarin Miƙewa take ya matse ta "Your perfume! Yana da daaɗi" Tayi murmushi "Thank you, gashi na mata ne da na baka" Dole ya saka shi dan murmusawa yadda take maganan bilhakki. Sun dan jima haka kan aka kira azahar ya sake ta ta mayar da kanta ƙasa tana wasa da bakin gyalen ta shi kuma yana kallonta. "Kin gama exams lafiya?" Tana mamakin yadda sai an manta wani abin shi kuma sai lokacin yake magananshi "Alhamdulillah" "Meyasa kika shiga toilet da waya kika jefa ruwa?" Ta ɗan zaro ido tana mamakin yadda aka yi ya sani shi kuma idanun yake kallo, haka kawai yaji baya so su daina maganan Dukda kanshi dake sarawa sai yaji in dai magana da ita ne ko za'a kwana kaman ba zai gaji ba, sanyin yanayinta, kamshinta, murmushinta da ma maganarta kashe shi suke. Bayani take mishi amma Bakinta yake kallo har ta gama bai ji komai ba, jin ana shirin shiga sallah ya miƙe ya nufi bayi bai ce komai ba, ta girgiza kai ta dauki tray ɗin ta fito dayake ɗakinshi akwai dan hanya tsakanin shi da parlor da hakan yasa tana gab da bayyana parlor ta ji Zarah na cewa Aisha "Aisha kina ganin Ya Sameer zai yarda ya aureni? Wlh tun ranar da ya cecemu na kamu da son shi da na fahimci shine Yaya Sameer wanda nake da alkawarin aure dashi tun yaranta sai na ji na sake kara sonshi kalleshi kiga yadda yake komai cikin wani irin aji da natsuwa...ba ki ji kishin da Naji ba da na kalli matarshi" Aisha tayi dariya "Zai aureki mana kin taba ganin inda aka yi alkawarin aure aka karya shi a zuri'ar nan? Kuma ai na ga matar tashi tana da sanyi bare ma dolenta ta ga kishiya har da kwarkwarori ma idan yana so sarkin gobe fa take aure" "hakane kam duk kishi na shiyasa nake dannewa sanin a auren sarki iya ruwa ne fidda kai kowacce ta iya allonta ta wanke ne, yanzu haka ba za'a rasa ma waenda suka nemi haɗin aure dashi ba ta wurin mai martaba daga bayyanar shi zuwa yau" Sossai maganganunsun ya daki Afeefah, bata san wani irin yanayi ta shiga ba ko motsi bata yi ba sai da ta ji ya buɗe kofa ya fito sai ya tsaya yana kallonta tayi kokarin danne abinda ke taso mata ta fita parlorn ya bi bayanta ya fice masallaci ita kuma kan ta isa dining ma kuyanginta sun karɓa... "Ba Za mu isa kuyi sallah ba?" Ta tambayesu tana danne yanayinta kwarai da gaske don for the First time a rayuwarta taji zafin wani duk abubuwan da ake mata a baya tana kokarin shanyewa kuma tana kokarin ta ga bata tsani kowa ba amma yanzu ji tayi bata son sake kallon Zarah a inda take, har ɗaci ɗaci take ji akan harshen ta maganan son da take yiwa Rayyan ke ta kai koma a ranta... "Kar ki damu yanzu za mu tafi ma ai" Kai ta gyaɗa suka miƙe suna mata sai anjima tace "Na gode sai anjima" Suka fice ta nufi ɗakinta ta samu bakin gado ta zauna tana dafa kirjinta dake zafi zafi, duk ɗan farin cikin da ta samu a tare da shi ya kau. Bata motsa ba sai da aka mata sallama ta ba da izini aka shiga sai ta kalli wata mata ce babbar mace rike da wani tray a hannunta wata kuyanga na binta a baya da akwati "Barka da wannan lokaci ranki ya dade" Nauyi taji na matar tace "Ina yini?" Matar ta kalleta lallai wannan ba tashin masarauta ba ce. "Fulani Faɗimatu ce ta aiko mu shirya ki mai martaba na son ganinku gabaɗaya" Kai ta gyaɗa matar ta shige bayi ta haɗa mata ruwa mai kamshin gaske ta mata iso cikin bayin ita dai ba don su jannah sun ce mata kar tayi musu a duk abinda ake sakata ba da zata ce musu ba sai ta yi wanka ba yanzu tayi wani amma kuma da ta shiga ruwan yadda aka hada shi ya mata daaɗi da ta fito kamshi duk motsinta haka yake tashi. Turaren kolecture suka bata mai bala'in kamshi ta shafa ko ina na jikinta kan ta shafa lotion ɗinta, da kansu suka shirya ta cikin atampha riga da zani da ya zauna mata sossai suka bata gyale ta yafa bayan sun daura mata dan kwali suka hada gyalen da ɗan kwalin suka yi pinning yadda ba zai dinga zamewa ba kan suka ɗora mata wani cream colour Alkyabba da yayi mata mugun kyau kaman ka sace ta ka gudu. Ta kara turaruka Dukda kamshin ma da take ya isheta, kan suka fito gabaɗaya ta samu su Abeeha a parlor "Masha Allah Kin ga yadda kika yi kyau uwargidan Ciroman fombina kuma Yariman matasan fombina?" Sai ta ɗan yi murmushi kadan don uwargida da aka ce ya tuna mata kalaman zarah.. Suka fice gabaɗaya aka musu jagora har babban parlorn mai martaba sun samu kowa na nan na kusa kusa dangi da ya kamata a ce sun sani. Gaisuwa aka yi Mai martaba ya gabatar da Uncle Musa da su Uncle sanusi matsayin dangin Rayyan tunda su suka rike shi tun barin shi gidan har kawo yanzu, yayi musu godiya marar iyaka kan ya nuna su Abeeha matsayin 'ya'yanshi don ya ce a yanzu basu da maraba da su Aisha a wurinshi sai ya nuna Afeefah don Ammi dake gefenshi duk ta nuna mishi su dama kuma ya riga ya gaisa da su Uncle kan zaman duk Ciroma yayi introducing nasu. "Ga 'yata Afeefah ita ce matar Ciroma, ina fata za mu cigaba da zama anan cikin zaman lafiya da haɗin kai yadda muke tafiya, ina marabtar ku da shigowa wannan masarauta matsayin 'ya'ya masu daraja, duk wani abu da kuke so za ku iya zuwa kai tsaye wurina dukkanku matsayin uba nake a wurin ku kaman yadda na dauke ku duk 'ya'ya na" Godiya duk suka yi Afeefah dai na matuƙar takure kuma zuciyarta bugawa yake kaman zai fito tana jin idanu sun mata yawa a jiki amma bata iya ta ɗago ba har sarki ya sallami Matan suka fice "Afeefah!" Ta ji muryarshi ya kira sunanta sai taji wani iri, sunanta a bakinshi daban take jinshi chak ta tsaya ya matso har tana jin kamshinshi da ma numfashin shi dake fita a hankali... "Ba na son duk abin da za'a baki a gidan nan ki ci! Idan ma ya baki sha'awa za ki iya fada min in nemo miki amma kar ki ci komai daga kowani bangare a gidan nan ina fata kin gane?" Kanta ya ƙulle ta ɗago ta kalleshi amma ganin idanunshi a kanta ya sa ta ɗan gyaɗa kai. "Ki amsa min da bakinki, bana son jin cewa kuskure ne ko akasin hakan... Ba kuma na so ki fara tunanin dalili hope am clear?" "In shaa Allah" Kai ya gyaɗa ya juya ya koma ita kuma tayi gaba ta samu su Jannah, aka fara raka su sashen Fulani Adama duk inda ta wuce kirari ake mata. A ƙasa duk suka zauna tana kame cikin kujera suka gaisheta ta amsa tana ɗan murmushi "ƴa ta Afeefah sai ga ki gidan sarauta, ina fata za ki ba da haɗin kai wurin ganin an zauna cikin aminci kin ga nan ba kaman normal gidaje ba" Tayi murmushi tace "In shaa Allahu Mama" "Sannan za ki yi haƙuri da tsare tsarenmu anan, duk muma haƙuri muka yi muke zaune lafiya ina fata in kin ji labarin alkawarin zarah da mijinki ba za ki ji haushin mu ba kar ki ga kaman daga dawowanshi ne aka bashi mata, kin san mu anan al'adar mu in aka haifi namiji da shekaru biyu ko uku ko ma biyar daga an haifi mace to za'a yi mishi alkawari wanda sai in mutuwa ce ta karya, kin ganni nan tun ban yi rarrafe ba nake matsayin matar mai martaba haka ma Uwar shi Ciroma amma kin ga duk muna zaune ne lafiya cikin amana da kula da juna" Ta Yi mugun ƙoƙari da ta iya danne hasalan da ranta ke yi tayi murmushi "Eyyaaa Allah ya ba mu ikon zama lafiya na gode". Sai kallonta Fulanin take har suka tashi suka fita ta sa aka bi su da kyautarta na maraba a ƙwarya rufe da faifai... Su Jannah maimaita maganan suke da damuwa ita dai bata ce musu komai ba har suka shiga wurin Ammi suka gaisheta "Afeefah kina lafiya kam?" Ta gyaɗa kai basu jima sossai ba don su Zarah suna wurin suka mata sallama itama kyauta sossai ta basu a ƙwarya suka nufi wurin Fulani Ameenatou kadaran-hadaran suka gaisa ta basu kyautarta suka nufi wurin Amarya Fulani Salimah itama suka gaisa kan suka nufi sashensu alkyabbar kawai take so taji ta cire ta huta gashi ana ta kiran la'asar, suna zuwa kuwa ta zame kayakin tas ta ɗauki karamar riga marar nauyi mai hannun singlet dogo ne sossai silk Brown ta saka yana da tsagu gefe da gefe har wurin gwiwa ta hau gado ta kwanta kawai bata motsa ba. Maganganun da ta riska yau kawai a gidan ta ji ya sire mata, bata san ta fashe da kuka ba zuciyarta na squeezing yana mata zafi ta ma rasa me ke damunta. Ta Yi kuka har tayi bacci a haka sai Magrib ta farka ta dauki hijabi ta saka bayan ta wanke fuskanta idanunta dai har lokacin sun dan kumbura kuma sun yi ja ta fito parlor ta samu su Abeeha suka ɗan yi hira ta ci abinci kaɗan kan ta ce musu za ta kwanta kanta na ciwo daga haka ta shige ɗaki. Abeeha tace "Addah jannah baki kula Afeefah na da damuwa ba?" Tace "Na kula Abeeha ko nima ina taya ta damuwa ace daga zuwa yau an fara mata zancen zata yi haƙuri mijinta aure zai yi, na san zai iya yi probably tunda dama haka tsarin su yake amma kuma bai kamata ana fada mata ba gaskiya." "Gaskiya sai Naji da ma bamu zo ba ni da nake murna, ashe abin da za mu tarar kenan ni haushina ma ko fa gama fahimtar juna basu yi ba." "Dole mu san abin da za mu yi akan hakan Abeeha, ki ji mana ko mu yi amfani da kishin nata ne mu ƙara kusanta su?" Shawara suka fara suna murmushi, Abeeha ta miƙe ta shige ɗaki jannah ta cigaba da zama don ita ce ma take dan iya magana da Rayyan ɗin ba tsoro ba komai tana nan zaune sai gashi kallo daya zaka mishi ka san ya gaji tiɓis. "Sannu da dawowa Yaya" Ya amsa da "Yauwa" Zai wuce tace "Wai da ma kai nake jira ne!" "Allah ya sa lafiya" "Da sauƙi dai Yaya Afeefah ce tun ɗazu take kuka wai kanta na ciwo ta sha pcm ma bai sauƙa ba" Ya ɗan yi jimmm yace "Meyasa baku kira ni ba? Kun san tana da low BP sai ta fara suma ne za ku yi aiki da hankali?" Da faɗa ya ƙarasa ta ɗan duƙar da kai "Ka yi haƙuri" Ya ja tsaki kan ya juya yayi ɗakin Afeefar. Ta saki murmushi ta juya ta nufi ɗakinsu Abeeha na jiranta suka kashe suna dariya har da kwaikwayon masifar shi, shi kam yana shiga.... 🖤Gureenjoh🖤 HAIHUWA DA HANJI (A True life story) Fatima Muhammad Gurin (Gureenjoh) Wattpad-Gureenjo6763 Arewabooks-Gureenjoh ADABI WRITERS ASSOCIATION *FREE BOOK* *50* Kai tsayen bakin gadon ya nufa ya kai hannu ya yaye duvet da take lulluɓe ciki, a hankali ya sauƙe hannunshi a goshinta hakan ya sa ta ɗan buɗe ido ta kalleshi sai ta mayar ta rufe, ta sake buɗewa idanunshi a kan wuyanta zuwa kan kirjinta da har saman ke a bayyane, muryarta yaji tace "Ya Saraki!" Sai ta sake mayar da idanun ta rufe, ƙarasa yaye duvet ɗin gabaɗaya yayi ya kai zaune gefenta yana kai tafin hannunshi ya shafa wuyanta da shima ya ɗan yi dumi amma ba zafi ba. "Kuka kika yi? Me ya sameki?" Shiru tayi bata buɗe idanun ba shi kuma bai daina shafa wuyanta da ya ɗauki hankalinshi sossai ba, jin yana ta da mata da tsikar jiki yasa ta kai hannu ta riƙe hannun nashi cikin wani irin murya ta sake kiran sunan nashi "Ya Saraki!" "Na'am Matar masu sarauta." Yadda ya amsan sai da ta buɗe idanunta, sunan ya shige ta har inda bai kamata ya je ba. "Mu je ki gayamin dalilin wannan kuka" Ko motsi bata yi ba, ganin ta ƙi motsawa Ya sanya hannu ya ɗauke ta chadak sai jinta tayi cikin hannunshi bai sake cewa komai ba ya fice da ita zuwa ɗakinshi, a kan shimfidadden gadon shi ya yi mata masauki zai kalleta don tunda ya ɗauketan a bazata kallon fuskanshi take tana jin soyayyarshi na shiga jini da bargon ta tayi saurin rufe idanu, bai ce komai ba ya miƙe yaje ya watsa ruwa ya sanya kayan baccin shi ya rage wutan ɗakin kan ya zo ya hau gadon ya kwanta. Duk abinda yake tana jinshi, kwanciyarshi da janyota zuwa jikinshi duk lokaci ɗaya hannunshi zagaye da kwankwasonta ɗayan a haɓarta ya furta "uhmm faɗamin" Da kyar ta iya samo kalmar "Mene?" Ta furta "Abin da ya saka Matar Saraki kuka har ya ja mata ciwon kai" Shiru tayi for seconds tsantsin rigar jikinta da kamshin dake fita daga jikinta har gashinta ya shagaltar dashi a hankali yake ɗan bin jikin nata yana shafawa ba tare da ya sake magana ba. Chan tace "Wai da gaske ku nan tun yaro na ƙarami ake mishi mata? Da gaske sarki ba zai iya zama da mace ɗaya ba?" Shiru yayi, chan ya ce "Wa ya faɗa miki wannan magana?" "Kawai na ji ne a wani labari..." Murmushi mara sauti yayi kishi ne ya sakata kuka kuma ya san tabbas faɗa mata aka yi don wulakanci daga zuwanta an tarbe ta da abin da zai sakata kuka a banza, kwafa yayi bai ce komi ba "Da gaske ne kenan?" Ya ji muryarta na ɗan rawa tayi tambayar. "Shhhh ki yi bacci, za mu yi maganan wani lokaci" Dole tayi shiru, hannunshi yake ɗan bubbugawa a bayanta kaman mai rarrashin 'yar baby har tayi bacci ya sauƙe numfashi yana saƙe-sake mai dumbin yawa har bacci ya sure shi shima a haka. Washegari ko da ya tashi sallah ya san bata yi so bai tashe ta ba, ya gyara mata kwanciya kan ya miƙe ya shige toilet yayi alwala ya fice masallaci, daga nan ya tsaya suka gaisa da su Uncle sun jima suna magana da Saleem da duk yau suke zancen juyawa, sai da gari ma yayi haske sossai ya dawo bai sameta ɗakin ba amma ta gyare tsaf ta saka turare ya tsinci kanshi da murmushi kaɗan kan ya wuce yayi wanka bayan ya shirya yana ma shirin fita ne ya ji sallamar ta. Ya amsa yana mayar da idanu kanta sai ya lumshe su ya sake buɗewa, yarinyar tana fusgar hankalinshi fiye da yadda zai misalta sanye take da wani coffee doguwar riga mai shige da material amma yana da kauri an tattare kirjin ƙasan a sake wane umbrella suna haɗa idanu ta kawar da nata don bata iya jure kallon cikin idanunshi barin ma in yana binta da mataccen kallon nan da ya tsira, gaban kujeran dake dauke da table ta ajiye mishi tray ɗin da ta shirya abincin kaman ka kwace don kyaun da yayi a ido, doya ne dafaffe da sauce na manja kana ganin kifi nasha nasha a ciki da kuma dafaffen kwai cikin Miyar, sai dafaffen plantain da ta musu wani yanka mai kyau, da tea mai kauri cikin mug sai da ta ajiye ta ɗago lokacin ya matso dab da ita. "Good Morning!" Ta faɗa har lokacin bata wani fara'a don ba wani daaɗin zuciyarta take ji ba, hannunshi na dama ya miƙa mata alamun su yi musabaha sai ta sanya nata ciki a hankali, da sanyawar da sauya hannun nashi da yayi zuwa hagunshi da fusgarta zuwa kirjinshi da zagaye kwankwasonta da yayi da hannunshi na daman duk lokaci ɗaya, kirjinta da nashi suka haɗe ta zaro idanu tana kallon shi shima cikin idanunta ya zubawa idanu sama da seconds biyu kan ya furta "Good Morning Caramel Queen..!" Ya faɗa yana bin smooth and silky skin ɗinta da wani irin kallo, kanta ta mayar ƙasa. Ya zame hannunshi dake kwankwasonta ya kai kan fuskarta da ta sako 'yar gashi kaɗan gaba ya ɗan shafa gashin da yatsa ɗaya yana mayar dasu gefe ya furta "Ya ciwon kan?" Ta kalleshi ta kawar "Alhamdulillah na ji sauƙi" "Har yanzu fushin ne?" Tayi shiru, ya ɗago haɓarta ya hura mata iskar bakinshi ta lumshe idanu, tana jin tender nd soft palms ɗin shi na wasa da tafin hannunta. "Talk!" Ta sauke nannauyar numfashi tana jin salon shi na kasheta, zamewa tayi tana zare hannunta "Abincin ka na sanyi" Haka kawai he doesn't like this silent treatment of hers. Zama yayi bai ce komai ba ta tura mishi abincin ya fara ci da bismillah ta juya ta fice, bayanta ya bi da kallo har ta rufo kofar ya sauke numfashi a lokaci daya yana tunanin wanda ya fada mata batun zarah shi da ko za'a shaƙe shi ma bai san kamannin zarahn a idanunshi ba, salon kishin ta kuma ya tafi dashi har yana dan murmushi wai ita tana fushi hmmm Misalin karfe sha ɗaya dukkansu suka fito don sallama da su Uncle Musa da zasu koma da Saleem, ita jannah na nan akwai wani taron Matasa da aka haɗawa Yariman na Matasa kuma Ciroman fombina wanda zallar al'ada suke son fitarwa a wannan gagarumin taron za'a yi shi a jibi sai gata sai ta wuce itama ta bar Abeeha da har sun fara batun neman transfer don Rayyan ya rantse ba gidan da zata je ta zauna kuma ba zata zauna hostel ba. Tun tahowarsu ya zuba mata idanu magana yake da Afeefah matsayin ɗan uwa da 'yar uwa yana kuma bata ƙwarin gwiwar zaman cikin gidan amma tahowar Aisha ya ɗauki hankalinshi har bai san kuma me yake cewa ba, Afeefah ta juya ta kalli wacce yake kallo haka ta saki murmushi ta juyo tayi waving "Ya Saleem ya dai?" Cike da dariya shima ya ɗauke kai ya mayar kanta "An tafi da ni ne, kanwata za ki taya ni yaƙi" Dariya tayi lokacin Rayyan ya ƙaraso inda suke har lokacin Afeefah na murmushi yace "Me yayi muku daaɗi haka?" Idanunshi a kan matar tashi da murmushinta ya tafi dashi ainun. "Sirri tsakanin yaya da kanwa" Inji Saleem, ta ɗan waro ido ta kalli Saleem tace "Gwara ka kiyaye aka hana ka babu ruwan Afeefah" "Da fa gaskiyarki, Yayanmu barka da fitowa" Ya juya yana miƙawa Rayyan hannu da kaman yanzu ne suka haɗu cikin ladabi. Murmushi Rayyan yayi yana girgiza kai wanda ya shagaltar da Afeefar a kallonshi don murmushi ne da bata taɓa gani yayi ba, murmushi na mishi kyau ainun barin ma fararen hakwaranshi da suka bayyana suka haske fuskar tashi. Gaisuwar da su Aisha ke musu ya sa ta dawo daga duniyar shagaltuwarta sai dai ganin kallon da zarahn ke yiwa Rayyan ya sa taji duk mood ɗinta ya chanza, shi kam Rayyan ko kallonsu bai yi ba ya amsa Uncle Musa ke yiwa Saleem magana akan su wuce kafin su yi missing flight dole duk suka yi wurin motar ya dubi Afeefah "kanwata za mu yi magana fa" Ta gyaɗa kai kawai suka yi sallama suka fice cikin motocin alfarma wanda da Rayyan suka tafi, su matan su uku suka yi sashenta suna 'yar hira yayinda Zarah da Aisha suka nufi ɓangaren Ammi. Rayyan bai tashi shigowa gidan ba sai yamma sossai, a parlor ya zauna ta kawo mishi ruwa ya sha hankalinshi duk a na kanta a koyaushe dressing ɗinta na kashe shi don yanzu fitted atampha ne a jikinta tayi ɗaurin ture ka ga tsiya da ya zauna mata tana kokarin ɗage tray ɗin gabanshi tace "Abinci fa?" "No sai anjima am not Hungry" Kai ta gyaɗa ta nufi kitchen shiganta ba jimawa tana ba kuyangin ta umurnin aikin da za su dan yi mata su yanke yanke na shirya mishi abincin daren bayan ta gama ta nufi fitowa daidai Gaabɗo ya shigo da wani paper bag ya zube a ƙasa "Ranka ya daɗe wannan saƙo ne daga Gimbiya zarah tace a baka" Da wani irin hanzari ya ɗago ya kalli kofan kitchen ɗin, bai taɓa jin tsoron wani ya ga ko yaji abinda babu daaɗi ba irin yanzu da yaji duk duniya tashin hankalinshi shine taji wannan zance. "Fita dashi, kar ka kara karɓan abu da sunan sako zuwa gareni matukar ba matata bace ko mahaifina" "A gafarceni ran..." "Fita nace!!" Da ɗan karfi yayi maganan da sauri Gaabɗo ya fice. Ya tashi shima gabaɗaya a parlorn ya wuce ɗakinshi a lokacin ita kuma ta fito hawayenta na zuba, Jannah da Abeeha dake daga chan jikin ƙofan ɗakinsu suka yi dariya. "Allah ya sa ta ji, don hakan ne kawai zai kawo musu kusanci idan tana kishin nan tana fusgar hankalinshi ne kanta" Jannah ta faɗa Abeeha tace "Amma kam za ki sakata kuka a banza Adda Jannah... Allah ka yafe mana baiwar Allah Zarah" "Eh gwara tayi kukan ta nemi mafita wa zuciyarta, ita kuma zarah dama kar tayi tunanin samun matsuguni a ran Ya Rayyan don shi ba namijin da zai iya da soyayya bane muddin Afeefah ta mishi dabaibayi a zuciya" Hirarsu suka cigaba da yi cikin nishadi don sun tabbatar ko Afeefah bata nemi Rayyan ba shi a yanzu ba zai jure nisantarta ba. Ɗakinta ta koma ta zauna bakin gado babu abin da bata saƙa ba kuma ta hana kanta kuka, dole ta yi me ɗungurungun wai haihuwa da hanji! Dole taje ta ji shin yana sonta ko da gaske baya sonta wata zai aura... Kiran Sallar Magrib ya sa ta miƙe ta gabatar da sallah don ta yi wanka tun rana, kitchen ta nufa ta haɗa mishi macroni da gasashen chicken breast tana cikin yi aka kira isha taje ta gabatar kan ta dawo ta ƙarasa taje ta shirya mishi a dining a yanzu hijab ne jikinta har ƙasa, daidai yana shigowa take cewa Sa'ade "Ki tattare kitchen nan please ban yi shafa'i da wutiri ba bari na gabatar" Bata ma kula da Shigowar tashi ba don ciki ciki yayi sallama ta wuce ɗakinta ya bi bayanta da kallo hannayenshi zube cikin aljihu, a natse ya ƙarasa dining ɗin daidai Fitowar Abeeha da Jannah suka mishi sannu suma suka zauna suka shiga cin abincin, ganin ta jima ya sa ya dubi Abeeha "ƙira min Afeefah" Ta miƙe ta nufi ɗakin ta samu ta idar tana zaune ne kawai, jin yana kiranta ta miƙe ta nufi parlorn zuwa dining. "Zauna ki ci abinci" Ganin fuskarshi ba fara'a yasa ta zauna ta zuba abincin kaɗan tana ci kaman bata so, karamin kwalin da bai jiman nan ba Gaabɗo ya zo ya ajiye mishi ya tura mata. "Na gode" Ta faɗa tana jan paper bag ɗin ta buɗe ciki sai ta ga waya ne dall a cikin kwali Iphone 17 Air ce, bata nuna zumudi ko farin ciki sossai ba sai ma su Abeeha ne ke ta santin wayan ta sake ce mishi ta gode ya bi fuskarta da kallo. Bayan sun bar dining ɗin su sa'ade suka zo suka tattare wurin tsaff. Ɗakinta ta koma ta bar su Abeeha da wayan a parlor suna mata setting ta yi wanka, ta duba wani orange and Black nigty silk ne mai hannun shimi ya bi jikinta sossai don Black lace ɗin ya kara haske kayan, hijabi ta saka a kai ganin yadda ko motsi tayi komai na jikinta na motsawa cikin kayan musamman hammatan dake bayyana tudun na shanunta time ta kallah almost nine. Fitowa tayi Abeeha ta bata wayan don jannah ta gudu waya da mijinta a ɗaki, ɗakinshi ta nufa kai tsaye da sallama ta kutsa kai rike da wayan a hannunta don tana so su yi magana. A tsaye take bisa kanshi yana kishingide cikin tattausan Italian cushion a hankali yake ɗan taune lip ɗin shi kaifaffun idanunshi zube bisa kanta "am...am just fed up, ba na tunanin zan iya cigaba da zama a haka i've had enough na san ba ka aureni ba ne saboda kana so na, ka aure ni ne out of pity da kuma am... Mammi. Muddin na cigaba da zama a haka zan iya mutuwa a yanzu bana jin zan iya cigaba da kasancewa matsayin ma..matar k..." "It's pretty!" Ya furta chan ƙasa cikin deep voice ɗin shi da ya sa ta kame, duk maganar da take yi ba idanunta yake kallo ba lips ɗinta da take motsa su a hankali ya ƙurawa lumsassun idanunshi yana wani kashe su yana buɗewa... "W...whatt?" "Ur lips... They are pretty" Ko kan ta farga ya yunkura ya fusgo hannunta guda ta tafi gabaɗaya kanshi tayi masauki a kan kafafunshi fuskarta ya sauƙa kan wuyanshi a tare suka ɗauke numfashi. A ɗan razane ta shiga mutsu-mutsun sauƙa ya sa hannunshi na hagun ya zagaye kwankwansonta yayi pinning ɗinta jikinshi, na daman ya sanya ya zare mata hijabin idanunshi na sauka kan jikinta, ya bi damtsen hannunta da yatsa biyu cikin wani salo har cikin tafin hannunta kar yayi baya ya riƙe wrist ɗin hannun ya ɗora saman heart ɗin shi da ke beating very very fast. A take nata ma ke ƙoƙarin sauya bugu numfashi na neman kwace mata idanunshi a saman fuskarta kaman zai tsagata da su ya furta "saƙon zuciya baki ne yake furta wa sai dai kuma wani lokacin yana iya fin ƙarfin harshe ya bar wa idanu nunawa, Lil angel saurari bugun zuciyata ki kalli tsakiyar kwayar idanuna na tabbatar sun isa sanar miki da cewa Ryan na ƙaunarki ba zai iya rayuwa babu ke ba, kuma yana tsananin buƙatar ki, you are like a Light in my darkness. You are not just my wife Afeefah you are my safe space, my solace...you are the key to my salvation..." Wani irin birkicewa ta nemi yi saboda nauyin zantukan nashi ga idanunshi masu kaifi da yake zagaye fuskanta da su yana wani lumshe su, maganar ma har cikin ɓargonta take ji saboda yadda muryarshi ke fita very deep nd husky. "A haka kike cewa in rabu da ke? Uhmm? Ki fahimta rashin ki a gareni masifa ne Afeefah" Ƙuri tayi da idanu kalamanshi suna samu matsuguni daram a cikin zuciyarta, sakinta yayi ta koma zaune kawai akan kafar tashi, kanta ta mayar ƙasa tana neman dulmiyewa tsabar yadda kalaman suke zuwa mata a bazata Rayyan ne fa gabanta shine yake fitar da waennan tsadaddun kalmomin daga cikin bakinshi? Anya ta ji da kyau? Ko dai yaudararta yake shirin yi ganin irin kallon da yake mata ba tare da ya sake furta uffan ba, shi ne zai so mace kamarta? Sake ɗago kai tayi ta kalleshi suka hada idanu. Sarai ya san kokonto take akan kalamanshi kuma hakan bai mishi daaɗi ba, ya kai hannunshi ya kama haɓarta ya ɗago fuskarta yana kallon cikin idanunta cikin karantar yanayinta bai furta komai ba. Idanunta ta mayar kasa zuciyarta na bugawa da tsananin karfi har tana jin kaman cikin ko wani lokaci zuciyarta zai iya yin bindiga ta mutu, amma shi ko a jikinshi kuma fuskar a kame yake magana idanunshi na yawo bisa jikinta ya ce "Idan kuma kin matsa da sai na rabu da ke, zan iya yin hakan ne kawai under 2 conditions Afeefah sai ki zabi wanda kike gani ya fi miki sauki ni kuma i promise zan rabu da ke!" A razane ta dago ta zuba mishi idanunta da har sun fara zubar da kwallah lips dinta dake rawa ya bi da kallo kan ya dauke idanu yana lumshe wa ya bude Da ma na sani baya so na tunda gashi zai iya rabuwa da ni amma me yasa nake jin zafi? Meyasa nake jin kaman karshen rayuwata ne ya zo? Abinda take ayyanawa kenan a ranta.. Da kyar ta iya furta "Menene conditions din?" Tana ji gwara ta sani gwara ta hakura ta nemi daidai ita. "It's either ki mayar da lokaci baya ki goge ranar da na fara sanin ki a rayuwarta don daga ranar ne zuciyata ta fara bugawa da Ƙaunarki ko kuma ki tsaga zuciyata ki sauya min da wata zuciyar don wannan ta jima tana sakar da jini mai dauke da kaunarki zuwa ko wani sashe na jiki da jijiyoyina...." Baki kawai ta saki hawayenta na zuba sossai da sossai, ya kai hannu ya janyota suka samu kusanci ainun, ya ɗago babbar yatsarshi ya shafa soft lips ɗinta dake ta rawa idanunshi na cikin nata yayi leaning a hankali ya ɗora bakinshi kan nata zuciyoyinsu na amsa baƙon yanayin nasu da karfin gaske....... 🖤Gureenjoh🖤 HAIHUWA DA HANJI (A True life story) Fatima Muhammad Gurin (Gureenjoh) Wattpad-Gureenjo6763 Arewabooks-Gureenjoh ADABI WRITERS ASSOCIATION *FREE BOOK* *Babu lallai ku ji ni da daddare manage this please, and na ga ruwan comments da Adu'o'i na gode kwarai Allah duk ya faranta mana ya hada mu da masu kaunar mu saboda Allah* *51* A hankali ya raba bakin nashi da nata, ya zuba mata idanunshi da suka matukar sauya ko da ta buɗe idanu sai suka sarke cikin nashin, ya riƙe natan sama da mintuna da suka fi biyu kan ya saukar da kanshi wuyanta yana goga mata gemunshi zuwa karan hancinshi a gefen kunnenta cikin wani irin salo da bata san ta mayar da hannayenta biyu bayanshi ta yi grabbing wuyanshi ba tana sauƙe numfashi. A hankali yake haurawa numfashinshi na sauka da zafi yana ƙarasa hautsina mata natsuwarta har ya isa cikin kunnenta cike da wani shauƙi mai dauke da mayen son da ba za ta iya resisting ba ya shiga whispering into her ears "Afeefahhh ke ce ta farko a zuciyata, ke kika buɗe shafin farko a soyayyata, a kanki jikina da zuciyata suka fara gamsuwa da cewa ni din namiji ne cikakke kuma ina buƙatar Abokiyar halitatta, ki amince min mu zama daya, ki yarda na baki ragamar rayuwata! dama ɗaya tak nake so ki ba ni...ni kuma zan killaceki a cikin zuciyata tsawon rayuwata, zan zama bawa a gareki mai hidimarki tsawon rayuwarmu zan tabbatar wa da duniya ke ce farin ciki na kuma hasken zuciyata..ina fata ba za ki hanani raɓa daga ni'imarki ba?" Hawaye ne ke zuba mata na rashin Makama, yanayin ya mata zafi kalaman sun mata tsauri ainun ta yadda take jin kaman tana duniyar halwa ne na soyayya ba duniyar mutane ba, bata san ta gyaɗa mishi kai ba yayi murmushi mai nauyi wanda sautinshi ya fita kaman numfashi, bata ankara ba taji ya tashi da ita a hannunshi ya isa ya mayar da hasken ɗakin dimmm sossai kan ya nufi gadon ya shimfiɗeta za ta yunkura ya bi bayanta his hands started to move inch by inch na jikinta, yana squezing ɗinta gently bakinshi is slowly kissing her and driving her nuts especially wuyanta da ya fi ko ina motsa shi, da baki yayi amfani ya saukar da sleeve na riganta cikin salon da bata taɓa sanin akwai shi ba, heavy breathes ɗin shi na sake birkitata. cikin natsuwa yake komai, Sai da ya tabbatar tayi laushi shima ya fara rasa kanshi a duniyarta kan ya nufi yin mai gabaɗaya, a sannan ne ya birkice ya gigice tunaninshi ya ɓace, jinshi yayi nisa bashi da buri a lokacin illa na ganin sun zama daya ta zama shi shima kuma ya zama ita, ko da ya ji shi a duniyarta ƙarasa haukace wa yayi a sannan ne ita kuma ido ya raina fata ta fahimci that pleasure da irin tarin iya sarrafa mace da yake dashi ne ya ruɗe ta har ta zaci abin mai sauki ne, duk irin magiya da roƙon da take mishi haɗe da kuka duk baya ji, idan hannunta ya sauka jikinshi ma sai yaji kaman zaburarwa ne cikin salonta. Bai sarara mata ba bai kuma saurara ba don yayi haukacewar da ko sunanshi ka tambaya a lokacin ba zai iya tunawa ba ita kaɗai ya sani, ita kaɗai kuma yake gani...Tsammmmm haka ya rukunkumeta yana binne kanshi a wuyanta a sadda ya samu cikakken natsuwa, Dukda irin halin da take ciki na fitar hayyaci da raɗaɗin azabar da bata taɓa fuskantar irinshi ba a rayuwarta tana iya jin ɗumin hawayenshi dake bin wuyanta, chan kaman daga wani uwa duniya take jin shaƙaƙiyar muryarshi na furta "Allah ya gafarta miki Mammi, Allah ya yafe miki kurakuranki Allah ubangiji ya sadaki da rahamarsa Allah ya jiyar da ke daaɗin aljannah fiye da yadda kika yi sanadiyar jin wannan daaɗi nawa na duniya....Thank you! Thank you Mammi" Sossai yake hawaye har numfashinshi na seizing ya mata riƙon da kaman ya tsaga jikinshi ya chusata yake ji ko zai samu saukin abinda ke shirin zauta shi, bai iya ya motsa ba kaman yadda itama bata da kuzarin ɗaga ko da yatsar ta ne, yana so ya ɗaga ta ya ji lafiyarta yana so ya gwada buɗe baki ko zai iya furta mata tarin irin kaunar da yake mata sai dai ya kasa, ya kasa sarrafa kanshi bare ya sarrafa jikinshi abu daya ya sani ta gigitashi a duniyarta ta goge mishi haddar da baya tunanin har abada akwai wacce ta isa ta kaishi inda ta kaishi, ta kashe mishi duk wani laka na jiki kaman ba tsayayye kuma jarumin sojan nan ba, ƙasusuwanshi sun yi laushin da ya kasa ko da lankwasa su bare ya sarrafa su har su miƙe a dole ya sake binne ta ya ja bargo ya rufa musu a haka wani irin bacci ya ɗauke shi ba tare da ya san halin da take ciki ba. Sautin kuka da turirin zafin dake fita daga jikinta zuwa nashi ne yayi sanadiyar farkawarshi, gaining courage yayi ya yunkura da ita a jikin nashi har lokacin banda bargon nan babu komai jikinsu duk su biyu, juyata yayi ta koma kwance yayi pecking goshinta a hankali ya fara ambaton sunanta "Afeefah... Bebe!" Bata amsa ba sai kananun kukan da take na zazzafar zazzabi idanunta a rufe kirib "Am so sorry...am sorry" Ya faɗa yana sake pecking goshinta kan ya sauka ya nemi wandonshi na bacci ya saka ya nufi toilet shi karan kanshi kafafunshi rawa suke kanshi ya mishi nauyi ainun, gefen cikinshi ya riƙe mishi sossai amma sanin dalili tunda shi likita ne bai wani damu ba ya haɗa mata ruwa mai zafi, ya dawo gadon ya ɗauketa kaman 'yar baby. "Matar Saraki..! Afeefah... Kina ji na? Zan saka ki a ruwa compose yourself kar ki ji zafin a bazata! Am so sorry Ya Saraki bai kyauta ba, Yafam boɗɗi am"(ki gafarceni kyakyawata) Da wani irin sloww tune yake maganan a kunnenta kan ya saukar da ita a hankali cikin ruwan, wani irin ƙara ta saki tana rirrikeshi za ta tashi ya shiga ciki ya danneta kawai ta kife kanta kirjinshi tana girgiza wa cikin azaba da kuka mai ratsa zuciya, hautsinannen gashinta da ya gama wargaza wa yake shafawa zuwa bayanta yana hura mata iska a kunnen yana whispering "sorry, am so Sorry My love." Sai da suka yi ruwa uku a tare tana liƙe bisa kirjinshi idanunta a rufe rufff kan ya sakata tayi niyya suka yi wankan tsarki, a towel fari ƙal yayi wrapping ɗinta ya sake ɗaukar ta zuwa kan cushion ya ajiye ta, har lokacin bata buɗe ido ba kuma bata bar kananun kuka ba shi kuma bai bar lallashi da ban haƙuri ba, gadon yaje ya chanza musu bedsheets. A gabanta ya tsuguna bayan ya ɗauko magani, bata ma san ya zo ba don har bacci ya fara fusgarta na wahala kawai taji hannunshi cikin towel ɗin ya shafa cikinta ta ɗan zabura sbd har lokacin hannunshi da sanyi ta buɗe ido sai suka haɗa ido tayi saurin rufewa yayi murmushi "Tashi ki sha magani 'yar albarka..!" Bata motsa ba shi ya ɗago ta zata fara kananun kuka ya sanyata jikinshi ya shiga bata tea din da ya saisaita zafin ta sha sossai kan ta sha maganin, a maimakon tayi shiru ma sai ta sake fara wani kukan. "Am sorry My love, har yanzu baki ji sassauci ba?" Ta gyaɗa kai tana hawaye don ita kaɗai ta san me take ji, shima kuma ya san jarumar mace yake tare da ita tayi matukar ƙoƙari, a hannu ya dauƙeta bai damu da su sa wani kaya ba suka koma kan gadon ya shimfiɗeta bisa kirjinshi "Sannu Chéri am(My darling) in duba in gani ko kina buƙatar stiches?" Ta maƙe kafada za ta fara kuka yayi murmushi mai sauti kan ya shiga shafa wet gashinta da yayi mishi laushin taɓawa saboda bai bushe ba, a kunnenta yayi whispering "Afeefahh kin san Bugawar zuciya alama ce ta mutum na raye ko? Toh kece bugun Zuciyata wanda hakan ke nufin idan babu ke a zuciyata babu ni zan iya amsa kowace irin tambaya a game dake saidai tambaya daya da ba zan iya amsawa ba ita ce wane irin so na ke miki, wannan tambaya ba zan iya amsata ba domin ni kaina ban san wane irin so nake miki ba abin da kaɗai na sani game da yadda nake jinki cikin jinina shine ba zan iya cigaba da rayuwa ba idan har ba'a tare dake ba. Afeefahhh idan har rayuwa ba za ta yiwu babu iska ba haka nima ba zan iya zama mai rai ba tare da ke ba, ke ce rayuwata Gimbiyata" Duk giyar soyayyarta ya saka yana jin kome ya faɗa mata yayi kadan wurin bayyana abin da yake ji, kuka take ba na bakin ciki ko ciwo ba kukan farin ciki take, tana kukan alfahari tana kukan isar ta macen da aka iya macewa a cikin begenta, tana kukan mallakar wannan gwarzo namijin da bakinshi bai yi nauyi ba wurin shimfide mata sirrukan zuciyarshi, rungumeta ya sake yi tsamm yana shafata cikin bege "Allah ubangiji ya kula min da dukkan lamuranki na rayuwa, yadda kika shayar da ni garɗi da zaƙin zumanki ubangiji ya shayar da ke ruwan alkausara... Thank you so much Habeebty a yanzu you are not just the part of my life you are the owner of my heart, ki yi bacci Habeebty kiyi bacci cikin salama" Da wannan kalamai haɗe da tarin lallashinshi mai tsadar gaske bacci ya ɗauketa. Ya jima sossai kawai yana kwance in ta motsa sai ya sake shigar da ita jikinshi kaman za'a raba su ne ya yi pecking tsakiyar kanta, sun so su makara don ƙarshen ta a gida ya ja su sallah bayan ya kaita tayi alwala, wani baƙin Oman jallabiyarshi mai adon gold ya saka mata sossai ya mata tsawo ya ɗauko mata hijab ɗinta ya saka mata shima ya saka jallabiya ya ja su sallah, suna idarwa ya janyota ta kwanta a kan kafafunshi ya zare hijabin yana shafa gashinta yake musu azkar duk su biyun don da kyar tayi Sallar saboda bacci da zazzabin da bai gama sake ta ba, tuni ta yi baccinta peacefully har ya gama ya dauƙeta ya mayar da ita gadon yana kallon pale fuskarta. Idanu ya lumshe yana sauke numfashi, a duk sadda zai ganta wani sabon ƙauna da mararinta yake ji yana kwarara cikin zuciyarshi, hannunta ya riƙo yayi pecking ya sake yi mata peck a Goshi kan ya miƙe ya fito, hadiman da suke share share da goge goge suka zube ƙasa suna kwasar gaisuwa, ya ɗan shafa kanshi ya ce "Ammm yau gabaɗaya na baku hutu, ina so ku koma sashenku kuyi duk abinda kuke so sai dare ku dawo" "Godiya muke Yariman Matasa! Godiya muke Ciroman fombina Allah ya kara girma da arziki Allah ya biya buƙatu" Kai kawai ya gyaɗa suka miƙe suka fice shi kuma ya nufi kitchen. Abeeha da zata fito kenan ta ji yana koran hadimai ta koma ta buga jannah da ke shirin komawa bacci "Wallahi barin sashen nan ya kama mu Addah jannah... Me afkuwa ta afku ga Ya Rayyan chan kitchen zai dorawa gimbiyarshi breakfast " Da sauri jannah ta miƙe zaune cike da zumuɗi tace "Keeee Ya Rayyan ɗin?" "Shi fa wallahi, hmmm ai na san jiyan nan ba lallai a wanye ƙalau ba, bawan Allah Saraki a waje Hadimin Afeefah a gida" Suka kwashe da dariya jannah na cewa "Kin ga irin su Yayan nan hmmm ki bar su kawai... Maza shirya bari nima na shirya mu koma sashen Ammi for today mu bar su su ƙone in sun ga dama" Abeeha na dariya ta shiga toilet wanka ji take zuciyarta kal kal, basu fi mintuna talatin ba suka bar sashen abin su. Shi kam bai ma sani ba yana kitchen, plantain yake frying amma minti minti zai saki murmushi yana tuna moments ɗinsu na jiya, ji yake ma yana kewanta a jikinshi daga Fitowar shi ɗakin zuwa yanzu, sai da ya gama ya haɗa mata spicy egg sauce mai ɗan yawa, ya yi toasting bread with butter very soft and simple kan ya shirya plate ɗin with so much love don burin shi kawai ya ga tana murmushi burin shi ya ga ta ji daaɗi kuma tayi alfahari, clean tray mai kyau garai-garai ya samu ya ajiye plate ɗin ya hada da tissue ko za ta bukata wrapped with cutlaries. Dube dube ya fara har ya samu wani drawer mai dauke da notepads masu yawa da Pen sbd specifying objects, rubutu yayi a jiki ya manna a gefen tray ɗin ya hada tea mai kauri sossai ya ajiye kan ya ɗauka ya nufi ɗakin. A gefen bedside ya ajiye ya yaye mata duvet ɗin har lokacin riganshi ne jikinta, ganin tana baccinta peacefully ya shafa fuskarta motsi ta fara a hankali har dai ta buɗe idanunta da suke kumbure ta sauke bisa kanshi ya sakar mata kyakyawar murmushi "Good Morning My Queen, My greatest blessing and the reason i believe in love..." Duk yadda bata so murmusawa ba sai da yayi escaping ta tsinci zuciyarta da dumbin farin ciki wane takarda. Miƙewa tayi zaune tana sauƙe kanta ƙasa haɗe da fara wasa da hannunta tace "Good Morning" Bai matsa mata ba ya san kunya ke ɗawainiya da ita shi ko a jikinshi ya ɗauko tray ɗin ya ajiye mata a kan cinya zai yi magana wayanshi ya shiga ƙira ganin mai martaba ne da kanshi ya sa yayi picking yana fita daga ɗakin don dole zuwa parlor. Note ɗin da yayi rubutun ta ɗauka ta shiga karantawa. "Na shirya miki wannan karin kumallon ne da tarin soyayya, kina da muhimmanci sossai a rayuwar Ryan. Allah ya albarkaceki da farin ciki da lafiya kullum, Ina ƙaunar ki!" Zuciyarta ta sa hannu ta dafe, kaunar ya mata yawa ji take ta ma rasa me zata yi sai sake karantawa take tana murmushi. Adanawa tayi ta dauki fork ta fara cin abincin da ya shirya mata da hannayenshi, loma biyu tayi sai gashi ya dawo yana zama gefen ta "Afuwan mai martaba ne ya kira ni ko yau zan samu fita ran gadi da shi" Kai ta gyaɗa tana sakar mishi cokalin bata ce komai ba don ya riga ya sanya hannu cikin nata ya karɓa ya cigaba da bata cike da kulawa yace "Kin san me na ce mishi?" Kai ta girgiza "Ce mishi nayi yau yini na, magana na da duk wata kulawa tawa naki ne ke kaɗai saboda kin bani abu mafi daraja a rayuwarki..." Da sauri ta kalleshi tana zaro idanunta waje gabaɗaya ya saki murmushi mai kyau har hakwaranshi na bayyana tace kaman za ta saki kuka "Da gaske haka ka faɗa mishi?" Hancinta ya lakace "Gashi na saka ki kallona da waennan idanun da suke kashe ni, kuma na ji wannan murya taki mai kaman sarewa..." Bata san tayi murmushi ba shima ya cigaba da yi har ya gama bata. "Mu je in miki wanka..!" Ta zaro ido "Zan iya wlh" Tayi saurin faɗa a Shagwaɓe ya kalleta "Ya daina zafi? Kin tabbatar za ki iya tafiya?" Kai ta gyaɗa ya dage tray ɗin ta sauƙo tana Miƙewa tsaye ta riƙo shi jin tana shirin faɗuwa wani Sharp pain na shigarta, ya ajiye tray ɗin yana saɓarta Duk rigima da Shagwaɓar da tayi ta mishi dole suka yi wankan ta lura ita ce ke mutuwa da kunya shi ko a gyalen shi tattalin ta yake wane ƙwai, shi ya dubo mata wani kaya ta saka Dukda ma ba masu nauyi ba a parlor ya ajiye ta ya kunna mata Tv wai tayi kallo bari ya zo, har ya tafi ya koma yaje ya ɗauko mata popcorn ya zo ya bata yayi pecking goshinta kan ya koma ɗakin nashi ta bi bayanshi da kallon ƙauna tana murmushi cike da tarin farin ciki.... 🖤Gureenjoh🖤 HAIHUWA DA HANJI (A True life story) Fatima Muhammad Gurin (Gureenjoh) Wattpad-Gureenjo6763 Arewabooks-Gureenjoh ADABI WRITERS ASSOCIATION *FREE BOOK* *52* https://chat.whatsapp.com/HUJI7tg9TOU941grP60r4S?mode=ems_copy_c Kinaneman group din dazaki ringa sarinkayan kitchen cikin farashin sari...tayadda koda kinje kasuwa bazakisamu kasa d farashinmuba snn zaki iyazuwa har hargida kisayi dukkan kayan dakike bukata cikin kwanciyar hankali kokisaya ayimaki delivery zuwa dukkan inda kike afadin Nigeria da dama makotan kasashenmu kikarbi kayanki cikin farinciki da aminci!!!.....kiyi joining a mai nono kitchen utensils and household........gaskiya d amana sune takenmu!!!👏🏻 ***** Ga mamakinta bai fita ɗin ba ya tabbatar mata da gaske yake ya cewa Abeey bata da lafiya ba zai iya yin nesa da ita ba, kunya ya rufe ta amma shi ko a gyalen shi da kanshi ya gyare ɗakin tsaff ya wanke beddings da suka ɓata kan ya dawo yayi joining ɗinta a parlor hannunshi da mug yana sipping tea, da kanta ta kai kwance jikinshi ya mayar da hannunshi ɗaya bayanta ya rungumeta suna kallon a tare hasken parlorn a kashe Dukda hantsi ce amma yadda curtains suke rufe kirib rip hasken duk a kashe sai ya ba da wani yanayi kaman cinema. Film din ya ƙare amma bata sani ba saboda ta yi nisa cikin tunani, hawaye kuma na bin fuskarta har take ji kaman zazzabinta zai dawo sabo, kula da hakan da yayi ya ɗaga mishi hankali ya ɗago fuskarta yana kallon ruwan hawayen da take yi "Afeefah lafiya? Me yasa kike kuka haka?" Yana maganan ne yana ɗauke hawayen da palms ɗin shi wasu na gangarowa, a hankali tace "Twins na cikin film din nan sun tuna min da Suhail da Suhaila ne, ko ya suke? Na san yanzu sun girma, ko suna maraicin uwa kaman yadda nayi? Ko suna samun farin ciki duk ban sani ba..." Fuskarta ya saka cikin tafukan hannunshi guda biyu ya matso sossai har suna shakar numfashin juna chan ƙasa cikin Muryar rarrashi yace "Ba kin rabu da su ba kenan har Abada Bebe..! Za mu koma in shaa Allahu za mu je mu gansu a tare ki daina zubar da hawayen nan, they are priceless to me..." Yana kai nan yayi leaning tare da fara ɗauke hawayen da harshen shi cikin wani salo da ya sa ta sake ƙanƙameshi, daga nan ya sauƙar da lips dinshi a kan nata da baya gajiya da su, sai da ta ga yana ƙoƙarin ɗaukar wani hanyar ta zame tare da kwanciya kan jikinshi ya rungumeta suna sauƙe numfashi a tare. "I love you...!" Ya raɗa mata a kunne, ta ɗan yi murmushi bata ce komai ba. "Na jima ina son na baki haƙuri kan wani laifi da na miki" Ta ɗan ɗago kanta tana kan jikinshin "Me kayi min Ya Saraki?" Ya kai hannunshi ɗaya yana wasa da gashinta da ya ki yarda ta saka hula idanunshi na a kan fuskarta yace "Ranar da kika fara gani na i scared you alot da har na kan yi sensing tsoron ki a duk sadda kika ganni ko kika ji muryata, that time i was very upset sai nake ganin kaman idan da akwai wanda ya fi cancanta da kashe kanshi ni ne but why you? Ƴar karama dake da wannan ɗanyen hukuncin? Raina ya ɓaci da na yi kwanaki da takaicin da ban san na menene ba, i wanted to go back to the hospital ko in kira Saleem amma na danne kawai ban yi hakan ba, daga baya i saw you at saleem's place da yake ba ni labari i was shocked sai dai sanar da ni da yayi yana sonki ya sa na miki murna a lokacin bcs na san shi mutumin kirki ne ƙwarai sai kuma matsalar mommy ya yi striking" Ta ɗan yi murmushi har lokacin tana kallon fuskanshi yadda yake magana da ma yadda yake wasa da gashinta na kara dulmiyar da ita a kaunarshi tace "Dukda na ji tsoro sossai da reaction ɗinka to tell the truth shine yayi sanadiyar gane kuskurena, reaction ɗinka ya fahimtar da ni ba karamin kuskure nayi ba a yunkurin kashe kaina da nayi... A lokacin bani da yadda zan yi Afeefah Mayya ce kuma annoba ce ba Afeefar yanzu ba" Yayi murmushi da yayi mishi kyau sossai "Har yanzu ma ai ke mayyar ce!" Ido ta zaro, ya kai hannu ya lalace mata hanci "Eh mana! Gashi kin lashe min zuciya" Bata san ta saki murmushi mai sauti ba tana ɗan hararanshi yayi pecking idanun yana sake rungumeta. "Ka san kuma da gaske na riƙe ka? Har ma sunanka marar kirki a zuciyata.." Ya ɗago ta ta zauna yana kallon fuskarta "Seriously??" Ta gyaɗa kai "Na fahimceka ne a sadda Mammi ta sanar da ni wanene kai!" Shiru yayi, ta sa hannunta ta riƙe nashi biyu "I hope yadda komai ya wuce a tawa rayuwar kaima za ka bar komai ya zama tarihi Ya Saraki!" Shiru yayi bai ce komai ba, ta san halin kayanta bata so tayi zurfi a maganan ranshi ya ɓaci amma ta fahimci yar tsamar da yake yi da mahaifiyarshi kuma rayuwa ba zai taɓa tafiya a haka ba, dole ne zai bar komai ya wuce kaman ba'a yi ba ta sani ba at once zai chanza ba amma a hankali dole zai wuce ɗin... Baya baya tayi ta jingina bayanta da jikin hannun kujerar bayan ta saka pillow sai ta wara mishi hannu, a hankali ya kai kwance kanshi na sauka a kan kirjinta ta saka hannayenta biyu tana shafa kanshi zuwa bayan wuyanshi shi kuwa ya lumshe ido yana ji kaman ya ɗauketa su koma ɗaki don kunna shi take ba tare da ta sani ba. Sun jima sossai a haka kan ya ce "Kin san mene?" Ta ce "uhm uhm" Tana cigaba da wasa da gashin keyarshi "I love hugging you, a duk sadda kika rungumeni sai na ji kaman mu dawwama a haka a tare, I just wanna lay here on your chest forever" Sake rungumeshi tayi tana jin kalamanshi masu tsada na sake samun matsuguni a ranta, ita kanta tana mamakin kanta amma an ce komai wuri yake samu a yanzu da yake nuna mata so da kauna sai taji she can go any extent don ganin ta faranta mishi itama, tsoron da take mishi ya kau sai taga kaman ba shine ke bata tsoron nan ba, kaman ba shine take shakkar ko tari a gangarshi ba. Suna parlorn har azahar ya fice masallaci ita kuma taje ɗaki tayi Sallarta, bata so ya dawo yace zai yi girki don haka ta wuce kitchen kawai daga ɗakin bata cire hijabinta ba don rigar jikinta wani iri yake sakata ji bashi da maraba da babu, har lokacin ba wai ta dawo daidai bane amma tana ga responsibilty ɗinta ne samar masa abinda zai ci. Mai ta ɗora a wuta ta kawo ƙoda da ta yanka 'yan daidai ta zuba, suna cikin soyuwa ta fara yanka sausage suma bayan ta kwashe kodar da ya soyu ta zuba sausage ɗin shima sai da yayi ta kwashe ta zuba shrimps da ta wanke tsaf ta soya su ta kwashe, ta kawo tomato patse ta zuba cikin man ta fara soyawa a gefe tana markada kayan miya da suke a frigde a gyare already sai da tomato din ya fara zaƙi kan ta juye kayan miyan a kai ta fara seasoning da su curry, chicken seasoning da dai duk abinda zata buƙata kan ta kawo soye soyenta na ɗazu ta zuba cikin sauce ɗin ta juya tare da rufewa ta nufi basmati Rice dake kitchen ɗin kofi biyu ta diba ta tafi bakin sink tana cikin zuba ruwa don wanke shinkafar ya shigo. "Kin yi laifi!" Ya faɗa yana nufarta, ta kalleshi ta saki murmushi "Tuba nake Ciroman duk duniya!" Hijabin ya zare mata ya koma ta bayanta yayi hugging ɗinta hannunshi ɗaya na zagaye kwankwasonta "Meyasa kike girki a yau? Ba ki san na haramta ba?" "Ba wani abu mai wuya bane kuma bashi da yawa, gashi na kusa gamawa!" Wuyanta yake shunshunawa "Shi wannan turaren kam kaman a fatarki aka haɗa so sweet" Ganin ya fara bata kisses a wurin ya sa ta ɗauki shinkafar da ta gama wankewa "Ya Saraki abincina zai ƙone" Bai saketa ba haka suka koma bakin gas din ta juye shinkafar ciki ya lumshe ido yana shakar kamshin "Hannunki daban ne a girki do you know that?" Tana zuba tafasashen ruwa madaidaici ciki tace "Lokacin da nake yi wa su Inna Larai Talla mutanen kasuwa kan faɗi hakan amma wannan training ɗin dai na abincin birni na same shi ne ta sanadiyar Mammi Allah ya gafarta mata" Ya ce "Ameen" Fuskarshi na nuna rashin jin daaɗin halin da ta taɓa tsintar kanta a baya, suna kitchen ɗin har ruwan shinkafar ya ɗan tsotse ta juya kan ta rufe da foil ta rage wuta ya kara 15mins ta juyo musu a plate ta ɗora kan tray shi ya Karɓa suka koma parlor, shi ya ɗauki spoon ɗin ya shiga bata yana ba kanshi, a lomar farko ya lumshe ido ya buɗe yana taunawa "Wow My love shi kuma wannan menene sunanshi?" Tayi murmushin farin cikin ganin yana yabon abinda ta dafa tace "Supreme Rice sunanshi" "I love it, Allah yayi miki albarka" Ta amsa da Ameen suka ci gaba da ci har suka gama ya bata ruwa ta sha kan ya tattare kwanukan za ta karɓa ya ture hannunta. "Ya Saraki..." Ya ma yi gaba bai saurare ta ba ta miƙe ta bishi "Kar fa a kama ni dumu-dumu da laifin saka Saraki aiki" Ya ajiye kwanukan yana ɗaukatarta gabadayanta "Girmanki ne hakan, ina so har abada in zama mai hidimta miki har sai na kasance ni ne ma'anar farin ciki a rayuwarki" She's just blushing daga jiya zuwa yau bata san matakin da zata ɗora farin cikin dake ratsa zuciyarta ba hakika tayi dace kwarai da masoyi, kai tsaye kan gadonshi ya shimfiɗeta ya zare rigan shi ya kwanta tare da janyota jikinshi sai ta fara zare idon tsoro. Fahimtar hakan don har a jikinta ya ji hakan ya sa yayi murmushi yana shafa kumatunta dake kan kirjinshi yace "Bacci za mu yi Gimbiya just stay calm okey ai na san baki warke ba, ko kin warke?" Kukan Shagwaɓa ta fara ya saki murmushi mai sauti yana shafa bayanta a haka suka yi baccin kuwa, basu tashi ba sai la'asar yanzu ma da kanshi ya mata wanka duk yadda take dojewa ya ƙi barin ta, gudu wa tayi ta barshi a bayin don ta kasa natsuwa yayi tashi wankan gabanta sai take jin kunyar duniya na rufeta. Ɗakinta taje ta shirya cikin wata atampha doguwar riga dinkin ya zauna mata tsaff ya fitar da duk wani sura na jikinta tayi wanka da turare isashe a ranta tana mamakin shine ya kori har su Adda Abeeha ko su ne suka yi tafiyar su yini guda basa nan, tana kokarin fitowa parlorn taji sallamar Gaabɗo sai ta koma don yanzu ranshi zai iya ɓaci. Shi kuwa ya fito ma ganin Gaabɗo ya sa ya samu wuri ya zauna sai ya koma Sarakinshi ya ɗora kafa ɗaya kan ɗaya yana relaxing ba tare da ya kalli Gaabɗon ba yace "Menene?" "Allah ya baka yawan rai kana da baƙo ne babba, na sanar dashi ka ce baka son ganin kowa yau amma ya dai tabbatar min lallai lallai in ce yana son ganinka" "Waye?" Ya tambaya yana kallon Gaabɗon don bai san wani isashen bane zai ce lallai lallai sai ya ganshi bayan ya ce baya bukatar ganin kowa a yau. "Allah ya baka yawan rai ranka ya daɗe Ameer ne na gidan Galadima" Da sauri ya ɗago "Ameer?" Kai ya gyaɗa cikin tabbaci "Kwarai da gaske ranka ya dade." ***** "Fulani kin yi shiru baki ce komai ba, tun da abin nan ya faru muke ta so mu zauna amma baki ba mu dama ba yau kuma kin kira mu kin yi shiru...! Kar fa mu tsaya kallon ruwa kwado yayi mana ƙafa shekaru nawa muka ɗauka muna shiri ba zai yiwu lokaci ɗaya komai ya warware ba. Ba zai yiwu ba" Ta kalleshi fuskarta babu ɗigon walwala tace "Baka kai ni damuwa ba Yaya, baka kai ni baƙin ciki ba... Ba kuma ka kaini takaicin dawowar wannan shegen yaron ba mai idanu a tsakar ka, ni kaɗai na san gwagwarmayar da ni tsawon shekaru ba zan ga kwaba na yana son yin ruwa in ja baya in zuba ido ba, sai dai ba na so mu yi gaggawa ne komai ya zo ya ƙarasa lalace mana! Dole za mu yi maganin abin" "A yanzu menene mafita Adda?" Ɗayan namijin yayi magana "Abu ɗaya ne tak, dole za mu gabatar da plan ɗin mu tun na farko a kanshi... A yanzu matsalarmu ɗaya ubanshi, amma zan san yadda zan yi dole ya amince da ƙudiri na mu kuma za mu yi amfani da daman mu salwantar da rayuwarshi da ta iyayenshi gabaɗaya don na tabbatar salwantarshi daidai yake da nasu salwantar don ba za su jure ba..." Ƙulle ƙullensu suka cigaba da yi sama da awa biyu suna nan zaune kan suka mayar da badda kamarsu suka fice daban daban kowa yayi hanyarshi. **** Yinin su Abeeha a sashen Ammi ya musu daaɗi don da kanta ma ta tsefewa jannah kai akan za su yi kitson Fulani tunda gobe akwai taron Matasa na Fuunange, hira suke yi sossai tun Aisha na ɗari dari da su har suka sake da juna Ammi kam kaman ta mayar da su ciki don kulawa musamman da suna bata labarin irin kalar rigimar Rayyan da Mammi suna ta raha da dariya. Ammin na jin kaman ta zama Mammi ko na seconds ne ta samu irin wannan kulawa da kauna daga yaron nata. Jin ma mijin jannahn zai zo goben yayiwa Rayyan ɗin ma murnan dawowa Ahalinshi sai su koma jibi yasa ta kira a zo a mata gyaran jiki na musamman, sai yau suka ji kaman sun samu madadin Mammi don duk abinda Mammi zata iya yi musu gashi Ammi na yi musu, bayan Azahar da kaɗan suna cin abinci ne ma an gama yi wa Abeeha kitson da yayi mata kyau ainun sai suka ji an turo kofar parlorn. Aisha ce ta fara kallonshi ta yi tsallen murna tana kwala kiran Ammi "Ammi! Ammi" Fitowa daga ɗaki Ammin tayi tana cewa "Aisha bakya rabo da autanci ihun nan fa? Sai idanunta ya sauka a kanshi fara'arta ne ya ninku a hankali ta isa ta kama hannunshi "Wa nake gani haka? Ko dai idona ne?" Yana dariya ya ce "Sam ba gizo bane nine Ammina, Na same ku lafiya?" *Kun ga readers marasa cewa thank you ko yin comment nan kuna bani mamaki, na faɗa pages dayawa a baya na nanata Weekdays ina da ayyukan dake gabana sai dare nake posting amma idan na kai daren nan su masu ma comments ɗin ainun da nuna jin daaɗinsu basa damuwa kaman Marasa cewa ko ci kanki..Allah ya kyauta* 🖤Gureenjoh🖤 HAIHUWA DA HANJI (A True life story) Fatima Muhammad Gurin (Gureenjoh) Wattpad-Gureenjo6763 Arewabooks-Gureenjoh ADABI WRITERS ASSOCIATION *FREE BOOK* *53* https://chat.whatsapp.com/HUJI7tg9TOU941grP60r4S?mode=ems_copy_c Kinaneman group din dazaki ringa sarinkayan kitchen cikin farashin sari...tayadda koda kinje kasuwa bazakisamu kasa d farashinmuba snn zaki iyazuwa har hargida kisayi dukkan kayan dakike bukata cikin kwanciyar hankali kokisaya ayimaki delivery zuwa dukkan inda kike afadin Nigeria da dama makotan kasashenmu kikarbi kayanki cikin farinciki da aminci!!!.....kiyi joining a mai nono kitchen utensils and household........gaskiya d amana sune takenmu!!!👏🏻 ******* "Ameer! Yaushe rabon da a gana? Ashe za ka zo?" Ya shafa kanshi yana rike hannun Ammin yace "Ammi abubuwan mu ne sai a hankali amma kuna raina wlh" "Da muna ranka ba'a waya kaɗai zaka dinga jin mu ba da kana zuwa shekara nawa rabon da ka waiwayi gida?" "Na tuba Ammi yanzu kam zan dinga zuwa, yanzu ɗin ma labarin bayyanar Sameer ya saka ni zuwa dole." Suka kai zaune, Aisha ta kawo mishi ruwa yayinda jannah ta gaishe shi ya amsa, Abeeha ma ta gaishe shi ganin shi mutum mai fara'a kwarai da wasa ya burge su. "Ammi ina kika samu wasu yaran babu labari?" "Ƙannenka ne, Abeeha da Jannah ga wani yayan naku ɗan wajen babban yayana ne Galadima, abokin Sameer ne don tare suka tashi kaman 'yan biyu a ɗakin nan ɓacewar Sameer bai sa ya bar nan ba anan yayi rayuwa har ya gama secondary ya tafi karatu chan kasashen turawa ya gama da jimawa ya ƙi dawowa" Sannu da dawowa suka sake yi mishi ya amsa da kulawa. "Ammi ina Sameer ɗin? Wani sashe yake?" "Ka ci abinci ka dan huta sai kaje yana chan tare da matarsa" Wara ido yayi "Har ma aure yayi abin shi" "Eh ya bar ku da gaurantaka" Yayi dariya, Abeeha ce ta taya Aisha presenting mishi abinci kan suka koma suka zauna suna ta jin hirar su da Ammi wanda suke tuna baya tasowarshi da Sameer, hakika zata iya cewa shine na uku a damuwar rashin Sameer don sai da yayi jinya tunda tun ba'a yaye shi ba ya yaye kanshi ya dawo wurinta saboda Sameer sun shaku sossai ta zama sanadiyar raba wannan ƙaunar. Bayan ya gama sashenshi da bai da nisa da nata ya ƙarasa don ana gyarawa akai akai kuma zaman cin abincin nan da yayi ta aika wasu hadiman sun sake kakkaɓewa ya tafi yayi wanka yana fitowa ma yaji ana kiran la'asar don haka sai da yayi sallah ya fita ya tambayi wasu fadawa suka fada mishi inda sashen na Sameer yake ya nufi wurin. "Amir Galadima..!" Rayyan ya faɗa fuskarshi ɗauke da fara'a shima Amir cike da fara'a ya rungume shi suka raba hug ɗin suka tafa irin na mazan dai da aka manta rabon da a haɗu. "Sameer kana duniya ashe? Baka kyauta mana ba! Ka ɓace babu traces? Hankalinmu ya matuƙar tashi har ka bayyana ban daina tunaka ba, saƙon bayyanarka na daga cikin news mafi jin daaɗi da na taɓa ji a duniya" Murmushi kawai Rayyan yake. "Mu isa ciki, wannan labari ne mai tsawo and ka san ban da bakin ba dashi" Suka nufi yana furta "Har yanzu ana nan da baƙin hali" Murmushi yayi yana tuna kalmar Afeefah wai ta mishi shaidar Rashin kirki a baya yace "Tunda matata ma ta faɗa hakan don ka faɗa ba komai bane" Dariya sossai Ameer ke yi har suka ƙarasa parlorn suka zauna, nan hira ya fara don Ameer na daga cikin waenda a bayan ma suka san dariyar Sameer, daga shi har mahaifinshi suna da muhimmanci sossai a rayuwarshi Dukda tun dawowarshi sau ɗaya yaje wurin Galadiman kuma tun da ya kawo mishi maganan Ammi bai sake komawa ba. Ita kam Afeefah jin hirar su yasa ta nemi gyale mai girma ta saka ta ɗora wata alkyabba marar nauyi shara shara a kai ta fito, tayi kyau sossai don ya kasa dauke ido a kanta Dukda bata shafa komai ba, gaisawa suka yi da Ameer cikin natsuwa da girmamawa kan ta kawo ruwa da su snacks ta ajiye mishi, ta kalli Rayyan "Ya Saraki bari na je wurin su Adda Abeeha yanzu za mu dawo" Bai ce komai ba don baya son abinda ke tsakanin shi da mahaifiyarshi ya shafe su dukkansu. Ta juya ta fice, tana tafiya ana jefa mata gaisuwa har ta kusa isa sashen suka haɗu da Fulani Adama, ta ɗan rusuna ta gaisheta "Lafiya ƙalau ya baƙunta Afeefah?" Ta amsa tana ƙare mata kallo ganin yadda ta sake wani kyau da haske. "Alhamdulillah Mama" "Masha Allah." Tana kai nan ta wuce ta itama ta wuce ta nufi wurin Ammin, zaune kuwa ta same su har lokacin ganinta yasa jannah fara cewa "Amarsu ta ango" Murmushi tayi tana sunkuyar da kai saboda Ammi dake wurin ta duƙa ta kwashi gaisuwa. "Lafiya ƙalau Gimbiya Afeefah, ya zaman baƙunta da rashin sabo?" "Alhamdulillah Ammi" "Masha Allah, yanzu kuwa Mamanku ta kawo min ƙararku sai dai na bata uzurin da cewa laifina ne tunda ku baƙi ne baku wani san tsare-tsaren ba, ni kuma rigimar Sameer ne yasa ban yi maganan ba" "Allah ya sa ba laifi muka yi ba Ammi" "A kan zuwa gaisuwa ne, ya kamata duk safiyar duniya ku bi ku gaida iyayen naku musamman ke Afeefah da kike matar Ciroma" "Ayi mana afuwa bamu san da tsarin ba amma za mu gyara in shaa Allah" Ammi tayi murmushi tana yaba Yadda Afeefar ta iya magana. "Adda Abeeha kitson nan yayi kyau masha Allah" "Kin ga nawa ni ma, kitson na da kyau wlh" Jannah ta faɗa tun kan Abeehar ta bada amsa tana nuna mata kanta. "masha Allah duk sun yi kyau" "Afeefah zo kema in tsefe miki sai a yi miki tunda duk gobe shigan al'ada za ku yi" Tace "Ai Ammi kaina a tsefe ne" Wacce ta yi musu kitson ta kira aka kawo kayan kitso na musamman itama aka shiga yi mata kuwa suna hirarsu. Dab Magrib aka gama yayi kyau ainun ya amshe ta don har a fuskarta zaka san ta chanchada kitso yadda ya ƙara sheki. Ana gamawa kuwa sai ga wani hadimi ya nemi a sanar da Fulani Afeefah Ciroma ya aiko a yi kiranta, Miƙewa tayi ta kalli su Abeeha "Adda Abeeha ku tashi mu tafi please" "A'a yi tafiyar ki muna wurin Ammin mu" Shagwaɓe fuska tayi "Ni kaɗai za ku bari a chan? Ammi kina jin su?" "Ba ke kaɗai ba kam, ki faɗi tsakaninki da Allah ko sanin mun taho ma kin yi in ba da kika ji shiru ba?" Hararar wasa take yiwa Abeehar suka yi dariya har Ammi ganin ta kasa cewa komai yasa ta juya zata tafi sai ta juyo ta kalli Aisha da itama sun fara sakewa sossai da juna tace "Ko za mu tafi kawai Aisha?" Aisha ta zaro ido "Ni?? Raba ni da shiga shirgin mijinkin nan yanzu su Adda Jannah suka gama labarin rashin mutuncinshi in je ya zane ni?" Zaro ido tayi "Yaya Sarakin ne bai da mutunci? A kunnenshi to!" Miƙewa suka yi suna ce mata ta tsaya ta ji ta rufa musu asiri su ba haka suke nufi ba tuni tayi gaba tana dariya suma duk dariyar suke har Ammi, saura ƙiris ta ci karo da Zarah suka tsaya suna kallon juna, a hankali maganganun Fulani Adama suka shiga dawo mata kaman yanzu suke yi, barin ma da ta ga kyaun da Afeefar ke ƙarawa ga iya ado kaman sarauniya, ga kamshin ta da in ka shaka zaka san ka shaka ko ita da ta tashi a masarautar bata irin dressing da daukar ido haɗe da kamshin da Afeefah ke yi, abinda ya sake sa taji kaman da gaskiyar Adama shine dariyar da ta samu duk suke wanda take da tabbacin yana da alaka da Afeefar idanunta ta sauke akan Aisha dake tsakiyar su Jannah sai kawai ta juya ta tafi. "Zarah kin tabbatar za ki iya aikata duk abinda za mu saka ki? Sannan za ki iya riƙe mana sirri?" "Mama kin raine ni ne akan kafafunki kaman ɗiyar da kika haifa da cikin ki, har manta cewa ni ɗin ɗiyar dan uwanki nake don ban taɓa neman abu na rasa daga wurin ki ba, don na taya ki yaƙi akan cikar burinki na tsawon shekaru ban faɗi ba sai ma halarci da na mayar. Dukda Na ji Son Ciroma Sameer a raina hakan ba zai hana na isar da Manufarki yadda ya kamata ba" "Masha Allah, haka nake son ji yanzu na san ban yi rainon banza ba. Zarah!" Ta amsa "Za ki auri Sameer dole sai dai bana so ko kadan zamanku yayi nisa" Kallonta take da neman karin bayani "Ba haka aka so ba kuma duk Shigowar wannan Afeefar ne ya ɓata mana komai amma a yanzu za mu gyara, za ki shiga a mata ta biyu amma ke za ki haihu za mu yi duk yadda za mu yi mu hana Afeefah haihuwa da Sameer, ke muke so ki sama mana ɗa namiji daga nan kuma za mu shafe Sameer" "Mama ko da yaron bai girma ba? To waye zai yi sarautar?" "Mahaifinki shine first cousin na sarki kuma yana da ikon yin sarauta zai iya riƙon ƙwarya har dan da zaki haifa ya girma ya bashi kin ga kenan Sarautar gabaɗaya ta dawo gidan mu kaman yadda dama tun chan yake a tarihi aka yi mana fin karfi aka hana mu" Shiru zarah tayi Fulani Adama tace "Ke kar fa ki tsaya wani kokonto don a sarauta babu kokonto ko tsoro, sannan kar ki bari wani soyayya yayi tasiri saboda babu wannan a tarihin jajirtaccun da suka yi mulki, ko ni na auri mai martaba ba don ina so ba sai don burin haifar Sarkin gobe, a yadda ban haihu ba na so kowa ma ya rasa har shi mai martaban ya mutu a haka dole 'yan uwana su karɓa amma Yarinyar chan Faɗimatu ta lalata min shiri don haka dole ne ta ga ba daidai ba" Waɗan nan sune maganganunsu da Fulani Adama da farko tana wasu-wasi amma yanzu ta ji lallai zata iya, za ta iya aikata hakan ba ɓata lokaci. Afeefah na isa ta samu yana zaune a parlor kafanshi ɗaya a kan daya yana ɗan karkadawa ganinta bai sa ya saki fuska ba tace "Barka da hutawa Ya Saraki" "Sai yanzu?" Ya faɗa yana kallonta, tuna irin kirkin Ammi take da irin damuwar da take ciki ko a murmushinta za ka iya fahimta hakan yasa ta miƙe daga inda take ta dawo kusa dashi tare da zame alkyabba da gyalen kanta haɗe da ɗan kwali tace a Shagwaɓe "Wai fushi ka yi na jima Ya Saraki? Kitso fa nayi kalli ka ga bai yi kyau ba?" Ya kasa ɗauke ido a kanta ta mishi kyau da Kitson sossai ya riƙo hannunta "vooɗi masin boɗɗiyel am" Dukda bata ji ba ta ɗan yi murmushi "Me ka ce kenan?" "Mai kitson Fulani bata iya yaren ba?" "Toh ai bana ji, kaima na yi mamakin yadda na ji kana yi fluently" Ta ɗan kwanta a jikinshi yana sake kallon kitson da ya fidda fatar kanta fesss yace "Tun daga ranar da na bar gidan nan ban sake yi ba sai da na dawo" Ta sa hannu ta zagaye cikinshi kanta na a kafaɗar shi duk tausayi suke bata daga shi har Ammin. "Toh ka faɗa min me ka ce?" "Ya yi kyau sossai kyakyawata. Abin da na ce kenan" Tayi murmushi mai sauti tana ƙoƙarin maimaita abinda yace da fulatancin, yadda ta shirmata dole ta saka shi murmushi har ma ya manta da yana kokarin yin fushi ne ta tafi sashen Ammi tayi zamanta. Bayan Magrib ya zo ya ja ta suka fice daga masarautar a wata BMW baƙa ya hana su Gaabɗo Binshi ta chanza zuwa wani blue Abaya da ya karɓeta sossai, shima navy blue Jean ne jikinshi da coffee shirt da ya fitar da hasken shi ainun sai ya saka facing cap navy blue saboda mutane baya so a gane shi a wajen don yanzu sai a fara maganan yana fita da kananun kaya, Sossai ya zaga da ita hannunta na cikin nashi yana driving da hannu ɗaya ba wani hira sossai yake mata ba amma in tayi magana yana kokarin amsawa bar shi dai da kallonta sai kuma pecking expecially bayan hannunta dake cikin nashi. Shopping sossai suka yi suka je suka ci abinci daga nan suka dawo suka sayi popsicle don tace tana so, sai wuraren 9 suka dawo gida hankalinsu kwance shi yayi sallah already ta shiga tayi nata kan ta shirya kwanciya, kaman jiya riga da wando ta saka masu yauki na kayan baccin cream colour da ya amshe ta sossai hannun rigan na singlet ta feshe jikinta yadda ya kamata, tsoron zuwa ɗakinshi take don bata san me zai faru ba kar a yi irin na jiya don ma shi likita ne yana da tarin sani akan yadda zai bi da ita ko da ta gurzu yayi jinyar kayanshi amma tana tsoron zafin don har lokacin tana jinta a kumbure. Gadonta ta hau ta kwanta shiru tana jin kewan jikinshi da har ta fara sabo da hawa, bata yi mintuna talatin ba ya tura kofan ya shigo ganinta kwance ya saka shi murmusawa ya isa gadon ya yaye rufan da tayi "Lallai ma yarinya ni za ki bari kaman gauro?" Dariya maganan ya bata ta kama murmushi Dukda yadda ta so tayi pretending ta yi bacci dole ya dauƙeta suka yi nashi ɗakin daga shi sai wani cotton wandon bacci chest dinshi duka a bayyane haka ya rufeta ciki, yana shafa bayanta yace "Wasu sun ce zazzafar soyayya tana zuwa ne a bazata! Na yarda Boɗɗi saboda a sadda na fara ganinki ban zaci zan so ki kaman yadda nake jinki a yanzu ba, ban san za ki zama abu mafi muhimmanci da daraja a rayuwata ba, I just fell in love with you and am still falling even harder cikin kowani dakika" Tana tare dashi amma tunaninta yake, tana a jikinshi amma kewanta yake bai taba sanin haka so yake ba, bai damu da yaji ta Bakinta ba shi dai ya san yana sonta daga shafata da yake ya nemi zarcewa, za tayi magana ya haɗe lips ɗinsu yana bata wani irin kyakyawar french Kiss da ya gigitata, tuni rigar ta yayi wani wurin ganin da gaske yake yasa ta kawo kuka ta saka mishi mai tsuma rai dole ya haura a hankali zuwa wuyanta yana ajiye wet kisses slowly ya isa kunnenta. "Am sorry boɗɗiyel am! Ki yi haƙuri kaɗan zan yi ba dayawa ba i promise ba za ki ji zafi ba" Girgiza kai take sai dai bai bari ta sake wani yunkurin ba ya shiga wasa da harshenshi a kunnenta, Tsam ta tsume sai da ya tabbatar ta gama rikicewa kan yayi abinda zai yi duk suka samu natsuwa cike da tarin soyayya da tsantsar kulawa kuma bata ji zafin kaman na farko ba, a tare suka yi wanka yau ma nade da towel kawai suka shige bargo yana sanya mata albarka a kunnenta haɗe da godiya. Washegari da safe kaman yadda Fulani Adama ta faɗa bayan ta gama mishi abin kari ya ci ya fita ma wurin mai martaba ta shirya ta nufi wurin Ammi don da gaske su jannah basu kwana sashen ba, bayan sun gaisa suka dunguma wurin Fulani Adaman suka gaisheta Madarar shanu ta basu akan su ɗuma ciki sabo ne da zafin shi, ita Afeefah bata sha amma don kar su yi laifi Jannah ta karɓa ta sha, Abeeha ma ta Sha Afeefah na ta wasa dashi har suka ce zasu tafi suka ajiye mata suka fice, sauran sashen suka je suka miƙa gaisuwa kan ta koma sashenta su jannah suka koma wurin Ammi. Bacci tayi sossai sai azahar ta tashi ta shiga shirya mishi abinci inda ta haɗa mishi White Rice da kidney sauce sanin yana son abin sossai, bata ma gama shiryawa ba ya dawo ɗakinshi ta kai ta ɗale kafafunshi yana ci yana bata har suka gama ta fitar da kwanukan. Bayan Magrib aka zo shirya ta zuwa wurin Taron da Matasan Fulani suka shiryawa Yariman nasu na murna. Kayan saƙi ne Fari aka bata ta shirya ciki a ƙasan rigan ta saka bodyhug mai dogon hannu fari ƙal kan ta ɗora rigan ya zauna mata sossai ta ɗaura zanin a ɗan sama kaɗan suka shiga cika mata kayan adon Fulani bayan an yi mata dauri mai kyau, goshinta, wuya, hannaye har kafa kayan ado ne irin na al'ada sai aka ɗora mata alkyabba fara kal tayi kyau sossai tana ta kallon kanta tana murmushi, bayan sun fita tana nan zaune sai gashi ya shigo. Miƙewa tayi tana kallonshi kaman yadda yake kallonta da tarin ƙauna, farin wando na saƙi shima shine jikinshi sai wani farin shirt kan rigar sakin har da hula yana rike da sanda yayi kyau har ta rasa wani irin kyau za ta ce yayi, wayanta da bata taɓa daukar ma hoto ciki ba ta ɗauko ta ja shi gaban door size mirror ta shiga yi musu mirror selfie, ya biye mata sossai akwai wanda ya ɗora sandar a wuyanshi ya riƙe da hannu ɗaya ya ɗan karkato ya ɗora hannunshi ɗaya akan cikinta bayanta na jingine a kirjinshi sossai posture ɗin yayi kyau amma bai yi dariya ba sai ta Shagwaɓe "Kayi murmushi mana Ya Saraki ka ga fa shiyasa ake cewa baka da kirki" Bai san yayi murmushin ba ta ɗauka duk hakwaransu waje da ya gaji ya ja ta suka fice tana kallon hotunan nasu na karshe daga ma baya ma shi ta mayar wallpaper wayan ya karɓa yayi air dropping shima ya mayar nashi wallpaper ɗin, sun isa katoton zallar filin taron dake cike da haske an kawata wurin da kujeru. Kusan kowa a wurin shirye yake da kayan saƙi na fulani sai a wurin suka haɗu da Jannah da mijinta shi Rayyan sun haɗu tun da ya fita da safe ita ce dai Afeefah sai lokacin ta ganshi, wurin yayi kyau sossai kujeransu na a haɗe, gefe yan mata da ƙwairen Nono da wasu kananu masu kyau a tsaftace wanda shine za'a sha a taron Matasa da yan mata cike da wurin kida da fulatanci na tashi daga wannan ya kare za'a saka wannan wasu na soyayyarsu yayinda Afeefah ke bin komai dake gudana da kallon burgewa, wasan kiwo da shanu aka fara inda aka ajiye shanu aka shirya Matasa biyar aga mai dabarar da zai iya tada shanu tsaye, sossai wasan ya kayatar bayan an gama shi aka yi shaɗi sai wasan Matasa na sanda, aka yi rawa kala daban daban su dai basu tashi ba Dukda ta so ta tashi amma ganin gogan ya ƙi bada dama sai ta natsu an saka waƙar wani mawakin Camero Jaamali Na Lara saftata ya waiga ya kalleta tace "Me ake cewa?" Ya ce "Zan fada miki sai mun je gida" Kai ta gyaɗa amma da aka kira wata mawakiyar Fombina Rukayya aka saka waƙar ta sai ya waiga ya kalleta "Akwai inda zan fassara miki amma da sigar namiji zuwa mace" Kai ta gyaɗa. "kin san me amshin ke cewa?" Ta girgiza kai "Ni fa ko zo in kashe ki aka ce ba sani zan ba bare na shirya guduwa" Murmushi mai kyau yayi hannunshi na cikin nata yana wasa dashi a yadda suke maganan kallo ɗaya zaka musu ka san masoyan Juna ne kuma exchanging kalamai suke don fuskarsu a sake musamman ita dake ta doka murmushi. Ya fara yi mata "Mi ɗon yidi ma a anda mi don yiɗi ma na? Mi ɗon yidi ma Yideyel am nder bernde am. (Ina sonki baki san ina sonki Ba ne? Ina sonki masoyiyata har cikin zuciyata)" Sossai take blushing tana jin kidan wakan na mata daaɗi barin ma rawan da Matasan suke. Bai sake magana ba sai da aka zo wani wuri yana wasa da hannunta idanunshi a kan fuskarta yace "Ki ji! Yiide ma nde nangi am mi warti bumɗo!(Sonki da ya kama ni na zama makaho) Yiide nangi am mi warti ginnaɗo..! (Sonki ya kama ni na zama mahaukaci) Waru nangam giɗɗo am saklare hosi am! (Zo ki riƙe ni masoyiyata jiri/hajijiya ya kama ni) Mi ɗo numa ma jamma be nange mi nyamataa! (Kina cikin tunanina dare da rana bana iya cin abinci) Mi ɗo numa ma nange be jamma mi ɗanataa! (ina aikin tunaninki rana da dare bana iya bacci)" Hannunshi ta sake gimtsewa tana sake faɗada murmushinta ta ce cikin yanayin 'yan koyo "Mi ɗon yidi ma a anda mi ɗon yidi ma naa mi ɗon yidi ma yideyel am nder bernde am" (Ina sonka baka san ina sonka bane? Ina sonka masoyina har cikin zuciyata) "Da gaske ko a waƙa?" Yayi tambayar yana ɗage gira daya cikin salo Ta saki murmushi "Da wanne kayi kai?" "Na taɓa miki wasan ina sonki? To ina sonki Afeefah! idan na kalle ki sai na ga cikakken kwanciyar hankali zuciyata ta samu natsuwa, kin kasance Abar alfarina!" A hankali in a whisper tace "Nima da gaske nake, ina sonka har cikin raina zan kuma zame maka macen da zata baka duk wani so da kulawar da ba'a taɓa baka irinshi ba, zan zame maka macen da ba zata taɓa ɓata maka da gangan ba, zan zama mai baka goyon baya a dukkan lamuran rayuwa, zan zama mai maka uzuri kuma zan kasance haskenka a duk sadda duhu ya nemi mamaye maka hanya, the girl you never want to argue with but communicate things out, the girl who love you for you ba don kudi ko mulki ba" Miƙewa tsamm yayi "Tashi mu tafi" Bai jira cewarta ba ya janye ta don tana cigaba da maganganun nan zai iya tafka abin kunya a bainar nasi duk nema take ta rikita shi ko ta kan Abeeha da ya hanga da Ameer yake so yayi magana bai bi ba ya buɗe mata ta shiga ya zagaya ya shiga aka ja su sai gida. 🖤Gureenjoh 🖤 HAIHUWA DA HANJI (A True life story) Fatima Muhammad Gurin (Gureenjoh) Wattpad-Gureenjo6763 Arewabooks-Gureenjoh ADABI WRITERS ASSOCIATION *FREE BOOK* *54* https://chat.whatsapp.com/HUJI7tg9TOU941grP60r4S?mode=ems_copy_c Kinaneman group din dazaki ringa sarinkayan kitchen cikin farashin sari...tayadda koda kinje kasuwa bazakisamu kasa d farashinmuba snn zaki iyazuwa har hargida kisayi dukkan kayan dakike bukata cikin kwanciyar hankali kokisaya ayimaki delivery zuwa dukkan inda kike afadin Nigeria da dama makotan kasashenmu kikarbi kayanki cikin farinciki da aminci!!!.....kiyi joining a mai nono kitchen utensils and household........gaskiya d amana sune takenmu!!!👏🏻 ***** "Duk wanda ka ga ya lashi zumar nasara, to tabbas ya ɗanɗani maɗaciyar haƙuri." Wannan ɗin wani zance ne na masu hikima. Bahaushe ya ce haƙuri gishirin zaman duniya, Yayin da ubangiji ya koya mana cewa duk inda abu ya je ya dawo kayi haƙuri! Duk ƙunci ka yi haƙuri, Duk damuwa ka zama mai haƙuri, Duk mai haƙuri shi ke galaba kuma duk mai haƙuri shi ke cin riba da wannan aya ta; "Ista'eenuu billahi wasbiruu" (Ku nemi taimakon Allah kuma ku yi haƙuri). Haƙiƙa da a shekarun baya za'a iya cewa zata taka wannan matsayi da take kai a yanzu za ta ce karya ne amma dayake Allah mai jin ƙan bayinsa ne da jiɓantar lamuransu gata a cikin ni'imarsa marar yankewa. Hakan ya sa cikin waennan watanni uku da suka biyo bayan tariyarta gidan Sarautar Fombina Bakinta bai taɓa hutawa da godiya ga ubangajinta ba saboda shi ya ce mana ka gode mishi a dukkan ni'imominsa shi kuma zai ƙara maka. "Alhamdulillahil lazee bini'imatihi tatimmus salihaat... Alhamdulillah ala kulli haalin... Alhamdulillah hamdan hamda... Hamdan katsiran dayyiban mubarakan fihi" Sun kasance kaman ruwan sha a Bakinta, ta samu duk wani gata da zata nema ta uwa irin Ammi da uba irin mai martaba. Waenda a yanzu suke tabbatar da cewa bata yi kuka da sunan maraici ba. Ta samu ɗumbin soyayya marar fasaltuwa daga wurin jarumi kuma gwarzon mazanta, a wannan watanni uku ba zata ce ko kallon banza ya taɓa shiga tsakaninsu ba bayan tattali da nuna kulawa, bata taɓa neman wani abu ta rasa ba zata iya cewa rayuwar da tayi a gidan na watannin ukun farko suna daga cikin waenda ba zata taɓa iya shafe su a tarihin rayuwarta ba, Dukda sau biyu yana tafiya akan aikinshi hakan bai dakile mata dukkannin abinda ya saba ba. Jannah ta koma sai dai su yi waya, Abeeha ta yi transfer ta dawo nan Fombina da karatun ta yayinda ta yi kane kane zuciyar Ameer Galadima ta hana shi komawa wurin aiki, a gefe ɗaya kusan duk waenda suke kusanci da Aisha da Saleem sun san cewa sun mato akan son junansu, daga mommy har su Sadiqa har Umman Sulaiman da ma matarshi su kan kira ta su gaisa sa'i da lokaci don yadda suka mayar da ita ɗaya daga cikinsu itama haka ta ɗauke su tamkar yan uwan da ta rasa, abu ɗaya ta kasa shine ƙarasa shirya tsakanin Rayyan da Ammi, yana da taurin zuciya irin na Fulanin Asali iyakancinshi da ita idan sun haɗu gaisuwa ne amma bayan nan baya ƙara komai Ameer yayi, mai martaba ya yi, Yaya Maudo(Galadiman Fombina) shima ya yi itama tana kan yi Dukda duk ranar da tayi maganan sai sun ɗan samu saɓani ya nuna mata baya so bata taɓa dainawa ba lokaci lokaci. A gefe ta kan tuna kawu da su inna Larai don an ce jini ko ya yake ya fi ruwa kauri duk abinda suka yi mata gashi bai katangeta da samun farin ciki ba, sai ma kusanta ta da yayi da farin cikin mai tarin alkhairai, Result ɗinsu na Waec ya fito kuma ta ci sossai tayi ƙoƙari Dukda shi gogan nata bai ce komai a kai ba hakan ya sa ta fara sanyawa zuciyarta cewa ba lallai tayi karatu yadda take so ba, ta sakawa zuciyarta ba komai kake so kake samu ba kila karatun ba alkhairi bane da haka ta danne ranta bata taɓa yi mishi magana a kan makarantar ba. Yau ya kama Friday haka kawai take cikin nishadi tun da ya sauƙe mata zallar madarar ƙauna ya fice da safe sa'i da lokaci ta kan saki murmushin da baya rabo da fuskarta, bayan tayi Sallar la'asar ta gabatar da duk abinda ta saba kowani juma'a a irin lokacin na karatun suratul kahf da adu'o'i ta tashi ta nufi kitchen. Ta ɓata lokaci sossai wurin gasa mishi kifi da yake matuƙar jin daaɗin gashin nata ta soya plantain da irish ta shirya table ɗinta tsaf kan taje tayi wanka, kananun kaya ta saka wando ne da bai kai ma gwiwa ba rabin cinya Black sai White Shirt da ta saka tayi wani irin kyau kaman ka sace ta. A kwanakin ita kanta ta san ta sake chanzawa ta yi kubul kubul fatarta yayi fresh kaman mai wanka da madara, ita kaɗai ce don tun gama taya ta aiki ta tura su Sa'ade sashen baya da ya sa aka gyara musu na cikin ɓangaren nata saboda shi ba mutum bane da yake son takura a sadda yake tare da iyalinshi, Abeeha ta jima da komawa wurin Ammi wai in ta cigaba da zama za su iya makantata cikin ko wani dakika don haka tayi ta kanta. fitowa tayi kai tsaye zuwa kitchen tana tuna wani haɗi na musamman da aka koya mata tun kafin aurenta dashi yau kam ta yi niyyar gwadawa, ayaba ta ɓare guda huɗu ta dauki tafarnuwa guda ɗaya ɗan daidai ta haɗa ta zuba a blender ta markade ta juye a cup, zumarta na asali ta zuba a kai tana jin haushin rashin kankanrar matar da bata dashi amma ko a haka ta san emergency ne mai kyau kaman yadda matar ta yabe shi, shanye wa tayi a tsaye a kitchen ɗin kan ta koma ɗakinta tayi ruf da ciki tana danna waya. Shigowar shi gidan jin bai ji motsinta ba yasa ya nufi ɗakin nata, sanye yake da khakinshi full don wani aiki ya fita akan tsaro tun safiyar yana tafiya yana ɓalle botiran ji yake kayan sun ishe shi, tura kofar ɗakin da kafewarshi a wurin lokaci ɗaya don ji yayi ruwan jikinshi na neman tsiyayewa, surar jikinta na neman zauta shi kafafunta zuwa cinyar ta dake a bayyane suka tasar da mazan dake jikinshi a lokaci guda, harshenshi ya fidda ya ɗan jiƙa lebanshi da yake ji sun bushe kan ya nufi gadon, ya ajiye kayan hannunshi ya kai zaune bakin gadon ya ɗora hannunshi kan cinyarta, tun shigowanshi kamshin turarenshi ya gaya mata wanene da gayya ta ƙi juyawan, ganin har lokacin bata juya ba ya sa ya saki murmushi mai sauti. Hannun ya ɗago ya kai kan rigan ta ya yaye ya kai fuskarshi yayi kissing fatar bayan yana shafawa a hankali, kan ya ɗan kwantar da kanshi yana jin yadda ta sauƙe ajiyar zuciya, bai yi magana ba ya cigaba da goga mata gashin gemunshi a bayan yana shafawa da hannunshi tuni ta kasa natsuwa ta juyo sai yayi mata rumfa yana haɗe goshinta da nashi ya lumshe idanu yana shakar daddadan kamshin turarenta dake ƙara hautsina shi. "Debbo boɗɗo am! Fushi kika yi?" (Kyakyawar matata) Yayi magana yana dan hura mata iska a idanun da ta rufe. "Shi ne ka je kayi zamanka ka manta da ni tun safe ko waya baka yi min ba.. Kuma ai ka ce za ka dawo da wuri amma sai yanzu? Kwalliyana har ya goge" "Ya subhallah...!" Ya ambata a chan ƙasan makogoronshin, peck yayiwa bakin Shagwaɓar ta sanya hannu akan dantsenshi dake bayyane don daga shi sai vest ya zame rigar ta riƙe shi da kyau. "Na isa in manta da bugun zuciyata? Ko kin san mintuna biyu a nesa dake kaman shekara biyu ne a gareni yayinda shekara biyu a tare da ke zai zama tamkar mintuna biyu? Sam bana sanin gudun lokaci idan ina kusa dake Matar masu sarauta" Murmushi mai sauti kaɗan ta sake da ta sake motsa zuciyarshi. "Ni ce addiction ɗinka yanzu kenan?" Tayi maganan tana ɗan yawo da hannunta slowly a kan damtsenshi zuwa ƙirjinshi, ya ɗan taune lip. "Yes you really are my dear.. Craving ɗinki nake kaman mai ciki" Dariya ta ɗan yi, ya kama lips ɗin da nashi yana kissing slowly kan ya saki ta ɗan yi murmushi "Always remember that zan iya gajiya da komai a wannan duniyar amma banda ke, even when am tired all i want is you.." Hannayenta ta mayar bayan ƙeyarshi tana mishi susa ita kanta ta san tana yin hakan ta gama kunnashi, tuni hannunshi ya kai ga kwankwasonta yana yin sama da rigar bakinshi is kissing her like his life depend on that, ba zai iya haƙuri sai dare ba he just want to feel her bukatarta kullum sabo yake zama mishi, kaman yadda mutum ba zai iya rayuwa babu iska ba haka yake jin ba zai iya rayuwa babu ita a gangarshi ba. Ya kuwa ɗanɗani abin da ba zai iya janyewa cikin lokaci kankani ba, rikice mata yayi sai da ta fara dana sanin shan abinda ta sha da yamman don bai barta ba sai da ta fara mishi kukan gaske, ya rungumeta yana sanya mata albarka. Tayi lub a ƙirjinshi suna sauƙe numfashi a hankali hankali, wayanshi ya duba sai ya ga dab ake da kiran sallah dole ya miƙe da ita zuwa bayi suka yi wanka duk jikinta a mace suka fito daure da alwala, bai iya ya je masallaci ba don an fara kiraye kiraye kan ya isa ma za'a iya idar wa jallabiya ya saka ya ja su suka idar, ya waigo yaga sai ɓata fuska take ya janyota jikinshi ta kwanta suka yi azkar a haka kan yana shafa fuskarta yace "Raguwata zan ga ranar da zaki gama sabo da jaruminki" A Shagwaɓe tace "Ni dai a'a na yi fushi!" Murmushi ya saki ta kalleshi "Murmushi na yi maka kyau kar ka daina kwata kwata ka ji Ya Saraki?" Yana shafa girarta yace "Yau jinki nake na musamman Boɗɗi garɗinki wane zuma farar saƙa don haka dole ma in yi ta miki har sai kin gaji. Tashi ki ga wani abu" Miƙewa tayi ya tashi yaje ya dawo manyan paper bags da ya shigo da su ya ajiye ya koma ya zauna, buɗewa yayi ya ɗauko wasu papers ya miƙa mata. "Congratulations wannan admission naki ne" Hannu ta sa ta rufe bakinta tana zaro idanu fuskarta cike da wani irin tarin expression tace "No..No you can't be Serious! Don Allah da gaske kake ko wasa? It can't be..." Ta ma rasa me zata faɗa tsabar farin ciki and ganin irin wannan tarin farin cikin da shine sanadin ya saka ya ji shima zuciyarshi ta yalwata da farin ciki, ta ajiye papers ɗin ta rungumeshi tana hawaye "Ban zaci za ka barni nayi karatu ba, har na cire rai ashe kana chan kana nema min thank you My love! Thank you so so much rabin raina" Ya rungumeta shima har ta gama farin cikin kan ya ɗago ta ya riƙe hannunta. "Maganan gaskiya Afeefah ina matuƙar kishinki, ina jin zafi idan na ga idanun wani namiji ya kalleki ko da da second guda ne, don ke ɗin tawa ce! don ni kaɗai aka halliceki kaman yadda aka halliceni don ke! At First ban yi niyyar bari kiyi karatu ba ko ba don kishi na ba sai don kasancewarki Matar Ciroma mai jiran gado, ba Girmanki bane chakuduwa da maza don neman ilimi hakan yasa na nema miki Open university" Sakin hannunta yayi ya buɗe jakar Apple Mac book ne da Apple Ipad ya fiddosu a kwali ya miƙa mata "za ki yi amfani da waennan kiyi karatunki daga kan gado i promise to help you in all the process exams kaɗai zai kai ki makaranta. Ina fata hakan bai ɓata miki ba?" Ts saki murmushi hawaye na zuba mata tace "Har wacece ni da zan ce hakan bai min ba? Ciroma ne fa gabana kuma Sarakin Fombina..! Ni din ban kai wannan matsayi ba kuma ko da na kai ba zan taɓa kin amincewa ba don ni'imace hakan da ban tsammata ba Allah ya bani, wasu na chan ma suna neman yadda za su yi karatun bai samu ba, wasu na chan suna yawo lectures cikin rana, zafi da ruwa ai ni daaɗina ma na samu miji mai gatanta ni... Allah ya saka maka da alkhairi na gode sossai na gode kwarai, na...." Bakinta yayi saurin rufewa da nashi ya bata deep Kiss da ya sa take jin sanyin na sauka har cikin zuciyarta. "Babu wannan tsakaninmu girmanki ne Sarauniyata" Tayi murmushi tana sake godewa Allah. Janshi tayi suka je ya ci abinci yana bata cike da kulawa har suka gama suka zo suka gabatar da isha kan suka shige cikin bargo yana yi mata setting na system da ipad ɗin yana koya mata yadda zata yi amfani da su tana daga kwance nashe nashe akan kirjinshi. Washegari da misalin ƙarfe goma ta fito cikin wani Apiligue lace peach da yayi mugun amsarta ta ɗora gyale mai girma a kai tare da alkyabba marar nauyi ta nufi sashen Ammi don miƙa gaisuwa, ta isa parlorn babu kowa don haka kai tsaye ɗakin Ammin ta nufa ta saka hannu zata bude ta ji Ammin na cewa "Yaya Maudo ni dai ban goyi bayan wani auren Zarah da Sameer ba Dukda na san alkawari ne amma Meyasa Mai martaba zai fara matsawa a yi shi yanzu? Shi kanshi Sameer ɗin ba son maganan yake ba sai kwana- kwana yake ya fi sati biyu mai martaba na Binshi da wannan magana... Ba wai bana son zarah bane amma yaushe har suka dawo suka gama sabo da nan ɗin? Kwata kwata aurenshi ma da Afeefar bai fi watanni takwas ba don Allah ka bashi shawarar a jinkirta ba dai sati biyu masu zuwa kaman yadda yace ba..." Wani irin faɗuwa gabanta yayi har tana ganin jiri, Dukda tana jin Ammin na cigaba da magana bata iya ta tsaya sauraronta ba don mugun jin da tayi ya daki zuciyarta fiye da zato ko tsammani, a gigice ta juya ta nufi sashensu don gaisuwar ba zata iya shi ba cikin wannan hali ta tabbatar da za'a bincika jininta yayi mugun hawa ko ya zuƙe tas yayi ƙasa tsabar tashin hankali Yana zaune kawai ya ga faɗowarta don yau din Asabar ne bai fita ko ina ba da kyar ma ya kyaleta ta fita gaisuwar, ganin halin da ta shigo ya sa yayi saurin Miƙewa yana rike kafaɗunta. "Afeefah! Afeefah menene? Me ya faru?" Ta kasa magana ma, girgizata yayi "Me ya sameki? Afeefah!!!" Da ƙarfi yayi maganan yana bin jikinta da kallo sai dai bai ga komai ba. "A wurin Ammie ne aka ɓata miki rai? Ko wurin Mama ne? Me ya faru kika shiga cikin wannan yanayin? Ki yi min magana mana!" Kuka mai sauti ta fashe dashi kaman wacce aka rufe da duka sai ta sake ɗaga mishi hankali ya juya da sauri zai fita ya tambayo uban da ya taɓa ta tayi saurin riƙo hannunshi tana kukan sossai duk ta ruɗa shi. "Sakeni in ba zaki faɗa min abinda aka yi miki ba Afeefah, Sakeni nace in je in ji dalilin da kaina...!" Da tsawa yayi maganan yana kokarin fusge hannunshi tayi saurin rungumeshi kamkam tana cigaba da kukan da ya ƙarasa cire mishi natsuwa. "I thought ina da muhimmanci a rayuwarka, a zatona duk wani abu da ya shafeka ya shafe ni Meyasa zaka min hakan? Meyasa Ya Saraki?" Sakinta yayi yana riƙo fuskarta idanunshi cikin nata "wa yace miki ba ki da muhimmanci a rayuwata? Kin kuwa san yadda nake jinki Afeefah? Meyasa za ki yi irin wannan tunanin?" "Ba gashi ba, idan har ka daukeni da muhimmanci ba zaka binne ni ba, ashe aure zaka yi nan da sati biyu? Aure Ya Saraki irin wannan baka iya ka sanar min ba?" Kukan da take na shaketa ta ƙarasa, sossai fuskarshi yayi Red ainun jijiyoyin kanshi duk suka miƙe kukanta tamkar saukar tafasashen ruwa ne a zuciyarshi shi kadai ya san irin abinda yake ji, a ina ta ji? Zai yi magana ta ture hannayenshi ta nufi ɗaki da gudu tana cigaba da kukan ya riƙe kanshi yana ambaton sunan Allah, bayanta ya bi da sauri sai dai ya tarar ta rufe kofan da makulli hankalinshi ya sake tashi ya shiga bubbugawa yana kiran sunanta cikin damuwa... 🖤Gureenjoh🖤 HAIHUWA DA HANJI (A True life story) Fatima Muhammad Gurin (Gureenjoh) Wattpad-Gureenjo6763 Arewabooks-Gureenjoh ADABI WRITERS ASSOCIATION *FREE BOOK* *55* https://chat.whatsapp.com/HUJI7tg9TOU941grP60r4S?mode=ems_copy_c Kinaneman group din dazaki ringa sarinkayan kitchen cikin farashin sari...tayadda koda kinje kasuwa bazakisamu kasa d farashinmuba snn zaki iyazuwa har hargida kisayi dukkan kayan dakike bukata cikin kwanciyar hankali kokisaya ayimaki delivery zuwa dukkan inda kike afadin Nigeria da dama makotan kasashenmu kikarbi kayanki cikin farinciki da aminci!!!.....kiyi joining a mai nono kitchen utensils and household........gaskiya d amana sune takenmu!!!👏🏻 ******** Yayi yayi ta buɗe kofar ta ƙi, har spare key ya ɗauko sai dai dayake ta bar key jikin ƙofan ya ƙi shiga, cike da damuwa ya koma ya zauna a kan kujera hannunshi dafe da goshinshi sama da mintuna goma yana nan shiru kan ya miƙe ya tafi ɗakinshi yayi wanka ya shirya cikin wani jumpha baƙi dinkin zamani, ya saka hula da half cover duk baƙake ya fito kai tsaye ya nufi motarshi su Gaabɗo na miƙa gaisuwa ma babu wanda ya amsawa ganin yanayinshi yasa basu nuna za su bishi ba don kallo ɗaya ya musu suka koma suka natsu. Tafiya ba mai nisa ba sossai ya kai shi shiyyar da Galadima yake duk a cikin masarautar, parking yayi ya sauka ya nufi ciki hadiman ɓangaren na ta miƙa gaisuwa bai amsawa ko ɗaya ba ya isa babban parlorn Galadiman, ya kuwa same shi zaune suna ma tattaunawa ne da Ameer, ganinshi ya sa duk fuskokin su suka cika da fara'a "A'ah yau ɓatan kai ka yi ne Ciroma?" Da kyar ya ɗan sake fuskan ya zauna "Baba Barka da rana" "Barka dai, ya iyalin naka?" "Alhamdulillah" Miƙawa Ameer hannu yayi suka gaisa kan ya dubi Baba. "Baba dama na zo ne akan maganan Zarah da mai martaba ya tayar, idan da hali ina so ka mishi magana Baba a dakatar da maganan nan zuwa gaba duk yadda zan mishi bayani ya kasa fahimtata, na amince mishi ne kawai saboda na san girman alkawarin wannan masarauta kuma ba na so ko kadan a ga gazawarshi ka san yadda su Makama suke... Na ji na amince amma ba yanzu ba kaman yadda suke so" Galadima ya sauƙe numfashi ya ce "Sameer da safen nan muka gama wannan magana da mahaifiyarka, ta kirani akan a ja maganan ba yanzu ba duba da baka ma wani jima da dawowa ba abubuwa dayawa baka gama sabo dasu ba, ga matarka da bata rufa shekara ba Dukda ba hujja bace tunda anan muna aurawa namiji ma mata biyu a rana ɗaya amma abin a duba ne zancen naku, Mahaifiyarka ba iya jayayya take da mai martaba ba a wanchan ɓangare kuma akwai Fulani da 'yan uwanta har biyu suna uzzura mishi duba da yarinyar ta isa auren shiyasa abin ya zo a hagunce. Zan gwada yi mishi magana idan ya amince sai a bar maganan for now amma da kamar wuya wai gurguwa da auren nesa" Idanunshi ya runtse ya san dama aikin su Fulani Adama ne they will be on his fathers neck har sai sun ga sun samu abinda suke so, shi wlh ba ma zai iya wassafa yadda zarahn take ba Dukda bata dameshi ba amma tashin Hankalin Afeefah shine abinda ba zai iya jurar gani ba a abinda ya shafi auren. "Baba don Allah a yi min wannan ƙoƙarin, mai martaba yayi rantsuwar ba zai karɓi wani uzuri daga gareni ba muddin ba mai ƙarfin da zai iya haramta auren bane a yanzu duk abinda zan fada mishi gani zai yi excuse nake kawowa na watsa mishi ƙasa a idanu" "Hakane. Dukkanmu ba za mu so ganin an yi ƙaranta ba don ba girman wannan masarauta bane, zan gwada mu gani" "Na gode sossai Baba bari na koma" Ya miƙe Ameer ma ya miƙe suka fito a tare a jikin motan shi suka tsaya yayi shiru. "Lafiya dai kam Sameer? Ko duk maganan auren ne ya saka ka cikin damuwa?" Numfashi ya sauke yana fesar da iska daga bakinshi "Ameer damuwana ɗaya ne tak tashin hankalin Afeefah, bana son zancen auren nan kwata kwata don na san ba zata ji daaɗi ba wace macece ce zata so a mata kishiya? Irin wannan kam ma Gani zata yi kaman don ita ba yar cikin gidan nan bane za'a ware ta ko a ba ni zarah, tunanin sakata a damuwan ya sa ban iya na yi mata maganan ba amma sai gashi ta ji a wani wuri yanzu haka tana chan tun dazu tana kuka ban san ya zan yi ba!" Cike da damuwa ya ƙarasa maganan. Kafaɗar shi ya dafa "Ban taɓa sanin haka rauninka yake ba sai akan Afeefah, kuma gaskiya baka kyauta ba ya kamata duk abinda yake faruwa ta fara sani daga wurin ka zata iya fahimtarka ba wai taji a wani wuri ba da ake maganan kila saura sati biyu...! Yanzu kai za ka kwantar da kai kayi rarrashin ta hanyar da zata fahimceka ko don gaba duba da kaine magajin wannan jaha ta mu ko a rana ɗaya ana iya baka mata a ɗaura bambancinta kawai zai iya zama kana sonta fiye da kowa kuma hakan ma wani makami ne a gareta" "Dole na Ameer don ba zan samu natsuwa ba muddin tana cikin damuwa, bari na je. Na gode" Da kallo Ameer ke Binshi har ya shiga motar ya bar wurin, murmushi yayi lallai So So ne hmm idan ba son ba wani abu ne zai taɓa zuciyar Sameer haka? Juyawa yayi ya koma ciki don basu gama tattaunawarsu da Mahaifin nashi ba. Sai da yayi azahar ya dawo ɓangaren ga mamakin shi ya samu abincinshi jere a kan dining kuma ya san bata taɓa bari hadimai su mishi girki ba kenan ita ta fito tayi, ɗakin ya nufa ya murda handle ɗin sai dai a rufe still goshinshi ya dafe bai taba sanin tana da fushi haka ba, ya san kalar haƙurinta lallai ya kaita maƙura. Dakinshi ya nufa don abincin ba zai shiga ba ya rage kayan jikinshi ya kai zaune yana lissafi. Wasa wasa har dare ta ƙi bude kofan, ko da ya fita Magrib da isha kan ya dawo ya samu ta ɗauke abincin dazu ta ajiye wani daban, shima bai bi ta kanshi ba ya sake komawa kofar ɗakin yana kiran sunanta amma ta ƙi ta buɗe daren tea ya sha daga ita har shi baccin su rabi da rabi don tunda suka shirya basu taɓa kwana ba tare da juna ba cikin bargo ɗaya skin to skin sai ranar. Ɓangaren Afeefah Da asuba bayan ta yi sallah ta ɗan yi azkar kan ta miƙe ta saka wani silk fabric gown ta ɗaura dankwalin fuskarta har lokacin da alamun kuka don kukan da ta jima bata yi ba tayi shi a jiya a ƙarshe ta yi finalizing solution ɗinta, ta sakawa zuciyarta haƙuri da juriya don ba zata taɓa hana shi ba idan Allah ya rubuta, haka ba zata saka ya ƙi bin umurnin iyayenshi ba ta riga ta sakawa zuciyarta cewa ko ba jima ko da bai auri zarah ba zai iya yin wani auren don haka za tayi Adu'a Allah ya kawo wacce za su zauna lafiya, za ta kuma yi iya kokarinta na ganin ta cigaba da zama ta farko a zuciyarshi har abada sai dai ba zata ɗauki ya dinga binne ta a komai ba, don yawan fushin nata ma na rashin faɗa mata akan lokaci ne. Ta zubawa dining ɗin idanu ganin bai taɓa komai ba ta tattare ta nufi kitchen ta saka a microwave don bai lalace ba, kokarin ɗora mishi wani abin take don ta san shi kam ba zai ci wanchan ba kawai ta ji an rungumeta ta baya, daga ita har shi sai da suka sauƙe wani nannauyan numfashi, shiru tayi bata ce komai ba ta cigaba da kokarin aikinta ya ɗaga ta chak yayi ɗakinshi da ita ya sauketa a kan gado yana zama ya riƙo hannayenta duk biyu. "Boɗɗi am...!" Idanunta ta kawar yayi murmushi mai sauti ya ce "Na tuba ki yafe ni Afeefah, ba zan iya jure fushinki ba Allah kaɗai ya san wani hali kika jefa ni daga jiya zuwa yanzu... Please lets talk kin ji?" Idanunta suka cika da kwallah bai ankara ba ya ji ta fashe mishi da sabon kuka a fili ya furta "Yaaa Salaam Afeefah...." Rungumeshi da tayi ya saka maganan yankewa, ya rufeta cikin jikinshi yana shafa bayanta idanunshi a rufe yana jin zafin kukan nata har ranshi. "Ki yi haƙuri na saka ki cikin wannan hali, it wasn't intentional ban san yadda zan iya fuskantarki da maganan bane but am sorry kin ji?" "Promise me Ya Saraki, ka min alkawarin cewa ba za ka taɓa juya min baya ba, ka yi min alkawari cewa ba zaka sake ɓoye min duk wani abu da ya shafe mu gabaɗaya ba, i felt hurt zuciyana ya kwana yana zafi da raɗaɗin jin zancen aurenka ba tare da na sani ba" Ɗago fuskarta yayi yana share mata hawayen da hannayenshi biyu cikin karyayyen murya yace "I promise Afeefah, na miki alkawari in shaa Allahu. Ki yi haƙuri i didnt meant to hurt you that badly dubi fuskar ki yadda yayi looking so tired and pale sbd zubar da hawaye" Wani hawayen ne ya gangaro sai ya runtse ido yayi shiruu. Shesheka ta ja ta sa bayan hannunta ta share wani ya sake zuba ta sake sharewa looking cute nd sad at the same moment. "Ka yi haƙuri i couldnt control my emotions ba laifina ba ne, am jealous kishi nake ji in na tuna nan da kwanaki kadan zan raba ka da wata, za ka shaki kamshinta ba nawa ba, za ka hada jiki da ita.... Am sorry" Duk ta rasa yadda zata yi bata san tana da irin wannan kishin ba kuma ruwan kaunar da ya zuba mata ya sa take jin shigo da wata duniyar su zai yanke mata wannan ƙauna. Jikinshi ya janyota zuciyarshi na tsananta zafi ya kasa magana, ita kuma ta zaci shirun da yayi ita ce take ɓata ranshi cikin kuka tace "ka taya ni Adu'a Allah ya sassauta min abin da nake ji Ya Saraki, am just jealous because I love you, angry because all i care about is you a lokaci guda kuma am scared because am afraid of losing you" Ɗagota kawai yayi ya haɗe bakinsu don kukan ya gama hawa kanshi, wani irin deep Kiss yake yi mata da tun bata amshi signal ɗin ba har ta amsa, a iya romance ya tsaya sai da ya tabbatar jikinta yayi laushi ainun fatarshi da nata na a manne da juna yana shafa bayanta a hankali suna sauƙe numfashi zai yi magana ta riga shi muryarta chan ƙasa tace "I wanted to be the only one to tells you I love you, wacce za ta haɗa miyaun baki da kai, touches your skin and feel you inside me sai dai kash! kana naka ne Allah na nashi, Kana da damar auren mata har huɗu tunda kana da halin hakan kuma kana da lafiya, abu daya zan roka daga gareka Ya Saraki kar ka daina so na don Allah zuciyata fashewa zata yi". Yana shafata tana sake yin lub jikinshi ya shiga furta "Afeefah ki yarda da ni, babu wata kishiya da zuciyar Ryan zata iya yi miki a soyayya domin ke ɗaya jal ta sani kuma ke kaɗai ta aminta da ki ja ta duk inda kike so, da ke kaɗai ta aminta a matsayin Abokiyar rayuwa ba ni da yadda zan yi ne da babu dalilin da zai sa in amince da batun zarah amma ba zan iya watsawa mahaifina ƙasa a ido ba alkawari ne da aka yi tun ban san kaina ba, amma in har za ki cigaba da wannan kukan komai zan iya yi ciki har da barin wannan gid..." Ɗagowa tayi ta haɗe lips ɗinsu da kanta sai da ta bashi kyakyawar Kiss kan ta kalli idanunshi hannunta na a fuskarshi shima idanunshi zube cikin nata da suke a rine tace "Kar ka ce komai, ni da kai duka karkashin ikon mai martaba muke dukkanmu uba ne shi a gare mu da magana kawai zai yi mu cika, sannan aure ba haramun bane idan yana cikin ƙaddararmu ina roƙon Allah ya ba ni haƙuri da juriya ya kuma kawo mana ta gari wacce za mu haɗe kai mu zauna mu kula da kai gabaɗaya, don haka Allah ya nuna mana lokaci ya bamu zaman lafiya gabaɗayanmu" Ta ƙarasa tana komawa kan kirjinshi ta kwantar da kanta tana mayar da hawayen da suka cika mata ido. Matseta yayi a jikinshi kawai bai ce komai ba, sun jima a haka don bacci ne ma ya ɗauketa shi kam bai iya yayi baccin ba damuwar da ta shiga ya tsaya mishi ainun ya san ba komai bane sai zallar soyayyar da take mishi, lumshe ido yayi kawai sai ranar da take ba Mammi da Abeeha labarinta ya faɗo mishi the way she was deeply hurt nd depressed anya ta chanchanci raba farin cikinta guda ɗaya jal da wata? Yayi adalci kenan idan ya iya haɗa jiki da wata mace ba ita ba? Numfashi ya sauke mai nauyi ya mirginata kwance ya ja mata bargo kan ya sauka ya dauki shirt ya saka ya nufi kitchen. Breakfast ya samar mata bayan ya gama ya kai har kan gado ya ajiye kan ya shiga shafa kanta zuwa fuskarta cikin tattali da kulawa har ta buɗe ido, murmushi ta mishi ya mayar mata "Tashi ki ci abinci Boɗɗi" Miƙewa tayi zaune tace "Brush tukuna bakina babu daaɗi" "Ba dole ba na tabbatar through out jiya baki ci komai ba" "kaima ai na ajiye maka baka ci ba i was disturbed" "Toh ba fushi kika yi da Sarakinki ba..!" Yayi maganan cikin muryarta ta saki dariya ya ɗauketa zuwa bayi tare suka yi brush suka dawo tana bashi yana bata har suka koshi. Wanka ma tare suka yi abin su yana ta takalarta tana ture shi, suka fito ta shirya shi kan suka je ɗakinta ya taya ta shiryawa. "Bari na je nayi gaisuwa na dawo" "Ki bar gaisuwan nan babu inda zaki a sake bata miki rai a banza" Idanu ta ware "An taɓa fushi da iyaye ne Ya Saraki? Iyaye musamman uwa ita kaɗai ce take mantawa da kanta yayin da take yiwa danta Adu'a ita a wurinta idan danta yayi nasara itama ta yi, Na san ka rasa Mammi ka kuma tabbatar babu zafi da ciwon da ya kai na rashin mahaifiya. Ciwo ne da baya taɓa goguwa har abada, zaka yi fata za ka yi adu'ar ko da ganinta sau ɗaya ne a yayinda kasa ya rufe idanunta a sannan kuma babu halin hakan, Uwa garkuwa ce ga dan da ta haifa, Ya Saraki in na ce maka ga kalar kukan da nayi na maraici ba zaka yarda ba, duk raɗaɗin da zan fada maka akwai ba zaka fahimta ba wani lokacin Allah ya sanya albarka daga bakinsu kawai kake nema ba zaka samu ba, Allah ya umurcemu da kyautata musu iya iyawa a sadda suke raye ni ka ga ban samu wannan damar ba, ko sanin su ban yi ba tsakanina da su Adu'a ashe ba zaka amfani wannan damar ba? Don Allah Ya Saraki ka sake tunani akan hukuncin da zuciyarka ke aikatawa, Allah ya sasanta tsakaninku cikin sauƙi" Shiru yayi ganin kaman zata ɓata mishi rai ta tashi ta fice tana ce mishi sai ta dawo ya bita da kallo kawai bai ce komai ba. Sashen Ammi ta fara zuwa suka gaisa ta ɗan jima suna hira da Zarah da Aisha kan ta wuce sashen Fulani Adama. "Barka da safiya Mama!" Tana hakimce ta amsa idanunta na scanning Afeefar ciki da bai kallon da ya sa taji duk ta tsargu kan ta amsa. "Lafiya ƙalau, shi mijin naki kam isar shi ta kai ya share sama da watanni a Masarautar nan bai taɓa zuwa inda muke ba sai dai mun haɗu a hanya ko? Uhm ko da shike ba ke ya kamata na yiwa zancen ba mai martaba ne ya ɗaure mishi kugu dole" Shiru tayi don bata san me zata ce ba, kiran hadimarta tayi "Ke Rahane kawo mata abin taɓawa" "Ai mama da ta barshi yanzu na karya kenan na fito" "Dama na lura baki taɓa cin komai na ɓangaren nan ba, ashe kema baki daukeni uwa ba kenan... ai shikenan sai gaisuwar ma a barta kawai Allahn da bai bamu 'ya'yan ba yana sane da mu, na ji labarin babu abinda bakya ci a sashen Faɗimatu nan ne ba zaki ci komai ba? Yayi kyau" Bata san Meyasa take mata maganganu haka ba, duk sai ta rikice ma tana tuna gargaɗin Rayyan akan kar ta ci komai na gidan kuma dai tana cin na Ammi, wani zuciyar yace ta gudarwa kanta matsalar Fulani Adama ta ci kawai ai Rayyan ba zai sani ba kuma ma kindirmon da aka kawo mata fari tas kwance a ƙwarya yayi matukar bata sha'awa don haka ta janyo ta dauki ludayi ta shiga sha, sai da ta sha dayawa ta ture tayi godiya kan ta miƙe ta bar sashen. Yinin ranar suna tare da Rayyan yana sake nuna mata ita kaɗai ce tauraruwar zuciyarshi yana cika ta da kauna don ko girkin rana da dare ma ba ita tayi ba, bayan sun gama cin abincin dare tana kwance kanta akan kafafunshi suna ma kallon wani movie ne yana wasa da gashinta ya shiga jin hannunshi na jikewa musamman in ya kai ga goshinta, shafa goshinta yayi yana kiran sunanta ta amsa "Lafiya kike zufa haka? Duk irin Ac dake aiki a parlorn nan?" Tace "Nima ban sani ba kawai dai cikina ke dan murda min kadan kadan ba sossai ba" "Mp ne? Amma ai bakya ciwon cikin priod pain tashi mu gani ko mu tafi asibiti?" Ta girgiza kai "Ba wani sosai bane ba fa zai daina Yaya" Ganin ta ƙi tashi ya sa ya kai hannunshi yana shafa mata cikin a hankali. Mutsu mutsu ta fara duk ta kasa kwanciya wuri guda ita kaɗai ta san azabar da take ji wanda rashin son tada mishi hankali yasa take ta daurewa, yana kula da motsinta sai gani tayi ya ɗagata ya kai hannu ya kunna hasken parlorn tarrr, ganin idanunta ya tabbatar mishi da ba ciwon wasa take ji ba. "Tashi mu tafi Asibiti" Ya miƙe yana riƙo ta bata yi musu ba ta miƙe tsaye sai dai abin da taji yana bin kafan ta ne yasa tayi saurin kallon wurin shima ganin yadda ta razana sai ya kai idanunshi wurin. "Jini??" Yayi maganan a ɗan rikice kaman kuwa ana jira su gani cikin nata ya shiga kartar da bai yi ba da farko, damke hannunshi tayi tana jin azabar na shirin kasheta tuni ta fita hayyacinta a rikice ya ɗauketa suka fice daga parlorn da gudu Gaabɗo ya je ya buɗe mishi mota ganin yadda suka fito ko tukin ba zai iya ba yana rike da ita a baya yana shafa cikin yana mata sannu sai juye juye take tana zub da hawayen da bata san suna ma zuwa ba, hankalinshi ba karamin tashi yayi ba jinin da bai san daga ina ba kuma na me na ta wanke su sai sannu yake maimaita mata kaman ya taya ta kukan a haka suka isa asibiti aka yi emergency da ita don har ta fara sumewa. A masarauta kuwa Ammi na zaune da su Aisha aka kawo musu labarin dukkansu hankalinsu ya tashi suka miƙe tsaye suna tambayar "Me ya sameta?" Babu wanda ya san amsar sai kiran me martaba da Ammi tayi tuni ya bata umarnin tafiya suka fito a ruɗe sai ga Ameer tare da shi da wasu securities suka bi bayan su Afeefar cike da adu'ar Allah ya sassauta koma menene ya bata lafiya cikin gaggawa.. 🖤Gureenjoh🖤 HAIHUWA DA HANJI (A True life story) Fatima Muhammad Gurin (Gureenjoh) Wattpad-Gureenjo6763 Arewabooks-Gureenjoh ADABI WRITERS ASSOCIATION *FREE BOOK* *Don Allah ku yi min uzuri na so in bi comments in amsa kowanne amma na kasa, bana jin daaɗi ne kar ku yi expecting biyu gobe in na iya na yi ɗayan ma Alhamdulillah!* *56* Afeefah ta matuƙar jiggata kan aka samu aka shawo kanta da kyar, shi dai ba zai ce ga abin da yake yi musu a ɗakin ba yana tsaye ne kawai saboda matsayin shi na likita kuma mai muƙami da ba zasu iya kora ba, hannunshi na rike da nata yana tsaye kyamm idanunshi na zube kan fuskarta wani irin ciwo ne wannan lokaci ɗaya? Me ya sameta? Babu kalar sake saken da bai yi ba. Kalaman da ya ji likitocin suke yi cikin harshen turanci cike da ƙwarewar aiki ya ƙara daure mishi kai ya jefa shi cikin tunani da damuwa lokaci ɗaya. "Sir da ka je ka sauya wannan kaya saboda duk sun yi stains, za tayi bacci sossai kila sai zuwa midnight ta farka sai a sake running wasu tests" Wani likitan ya faɗa bayan ya dafa kafaɗar Rayyan da ya jima cikin duniyar tsoro, mamaki da kaɗuwa. Hannunta ya zame yana kallon kayan da aka kawo za'a sauya mata da wasu towels da za'a goge mata jikin da ya ɓaci Dukda mata ne karɓa yayi suka fita, shi ya goge mata jikin tas ya sanya mata kayan asibitin riga da wando ne kan ya gyara mata kwanciya ya duba tafiyar ruwan har lokacin fuskarshi Jajazir, kwakwalwarshi ya ƙi hutawa da saƙe saƙe a haka ya fito daga ɗakin sai ya tsaya chak yana kallon Ammi da take kallonshi itama a zaune. Jikinshi ya bi da kallo yana tuna jinin ɗan shi ne nan ko ɗiyar shi, wani irin zafi da bai san ya zai fasalta ba na taso mishi a cikin zuciya bai san ya nufi Ammin ba ya samu wuri a gefenta dab ya zauna bai ce komai ba kanshi a ƙasa, dukkansu sun yi mamaki har ita kanta amma ta danne tace "Sameer ya jikin Afeefahn?" Ya yi shiru na seconds yana hadiye wani irin miyau ya ce "Da sauƙi tana bacci" Wannan ne karo na farko da maganan da ba gaisuwa ba ya shiga tsakaninsu hakan ya faranta mata kwarai amma damuwar halin da Afeefah take ciki bai barta ta nuna ba. "Me ya sameta haka?" "Ammi Afeefah ta ci wani abu a sashenku da safe?" Abeeha da har hawaye tayi ta zubarwa tace "A'a Yaya ko ruwa bata sha ba tace ta ci abinci kenan ta fito" "Me ya faru da ita haka?" Ameer da Ammi suka tambaya a tare, haƙorinshi ya sa ya datse lip dinshi na ƙasa kan ya saki zuciyarshi na tafarfasa yace "Ɓari tayi... Zubar da shi aka yi! ta yi misscarrage ba tare da duk mun san akwai ma ɗan ba.." "Innalillahi wainna ilaihi rajiun..." Abinda duk suka faɗa a tare kenan, Ammi ta sanya hannunta ta kama nashi sai ya kalleta "Ammie ɓari biyar kika yi?" Ta gyaɗa kai bata ce komai ba "Duk wannan azabar da Afeefah ta sha haka kika sha?" Ta sauke numfashi tace "Na sha wanda ya fi shi ma Sameer, shi ina mai tabbatar maka azabarshi zai iya ɗara na haihuwa. Ka je ka sauya kayan nan haka kar ƙarnin jinin ya zauna maka a jiki" Idanunshi ya ɗaga sama yana mayar da emotions dake taso mishi ya kalli jinin "Ɗanki ɗan watanni biyar ma kin rasa shi ko Ammi?" Nan ma ta gyaɗa mishi kai. "Haka zafin yake?" Bata danne ba tayi murmushi mai ciwo tace "Duk wanda za ka ji daban yake da na uwa Sameer, uwa ce kaɗai za ta iya fasalta wannan zafin... Idan har ka ji zafin fitan ɗan da baka ma san da zamanshi ba ka fasalta da Aliyu da na rasa sai da na raini cikinshi na watanni tara na haife shi na shayar dashi na ga haƙorinshi na farko, na ga murmushinshi na farko na ga zamanshi kan Allah ya karɓi abin shi..." Hawaye ne ya zuba mata a lokaci ɗaya da Ryan, shi likita ne amma bai taɓa kula da abinda ya shafi ciki ko haihuwa ba don duk abu da mata a baya ba kaunarshi yake ba, cikin jannah da Abeeha duk ba zai ce ga yadda Mammi tayi ba, idan wannan bari ya saka shi jin irin wannan zafin ya Ammi ta ji? Bayan duk wahalar kuma aka yi ta yunkurin kashe shi mahaifinshi bai ɗauki kwakwaran mataki da zai sa hankalin uwar tashi kwanciya ba, motsin da suka ji yasa duk suka ɗago sai ya ga mai martaba ne da dogarai biyu don ya kasa zama dole ya biyo bayansu. Shima kuma a yanzu ya fahimce shi dole ba zai so rabuwa da ɗan shi guda da Allah ya bashi bayan tsawon shekarun da ya ɗauka babu haihuwa ba. Dukkansu basu da laifi, uwar da ta zama distressed ta haɗa baƙin ciki, damuwa da wahala duk lokaci guda zai ga laifinta ko uban da baya so ya ga yayi nisa da gudan jinin da yake mararin samu? A yanzu ya fahimci damuwar Ammi ta sanadiyar Afeefah ya ji a ranshi zai mata uzuri ya ji a ranshi kaman Allah ya riga da ya rubuta ne Mammi ce zai yi rayuwa da ita har mutuwar ta ba Ammi ba, kaman yana ji a ranshi cewa Adu'ar Ammi ce Allah ya karɓa ya tura mishi Mammi. Ta wani ɓangaren he's grateful na barin shi masarautar don da bai bari ba da bai san Mammi ba idan kuma bai santa ba da bai samu Afeefah ba the 2 most important persons da Allah ya bashi su as his greatest gift. Ƙasa ya kai ya riƙe hannun Ammi ya ɗora fuskarshi a kai ya ce a hankali "Ammie ki yafe min, ki yi haƙuri na tuba!" Ɗumin hawayenshi suna sauka ne da nata, kuka take sossai na farin ciki Allah ya amshi adu'ar ta, Allah ya karkato mata da hankalinshi cikin sauƙi. Ɗago shi tayi ta miƙe tsaye kawai ta rungumeshi Dukda tsawon da ya fita, duƙawa yayi suka rungume juna yana jin dumin mahaifiyar tashi na ƙara karya zuciyarshi, da kyar ya danne kukan da ke taso mishi. Mai martaba ya dafa shi yana dan buga kafaɗar shi zuciyarshi fari tas na ganin abinda ya jima yana fata shima, komai ya wuce don Ammie ɗago shi tayi ta ce "Sameer na yafe maka duniya da lahira baka yi min komai ba, ni ya kamata ma in nemi yafiyarka da wahalan da na saka ka... Haƙiƙa na yi kuskure mai girma wanda Allah ne ya dube ni ya raya min kai kan tafarki amma da ban san da wani ido zan isa ga mahallici na ba da rayuwarka ya salwanta. Ka yi haƙuri" Kai ya gyaɗa. Mai martaba ya ce "Ya mai jikin yanzu?" Cike da girmamawa Ammie tace "Alhamdulillah Taƙawa tana bacci ne sai dai mun rasa ɗan cikin" "ɓari tayi? How?" Juyawa Ryan yayi ya fita Ameer ya bishi, Ammi ce ta mishi bayanin suma basu sani ba amma da yake asibitin kuɗi ne kuma kwararrun likitoci ne suka duba ta a bincikensu sun tabbatar da abu ta sha yayi sanadiyar zuban cikin. "Tirƙashi! Kar fa tarihi ya maimaita kanshi!" Shiru Ammi tayi ba zata so wa Afeefah wannan wahalar ba, Amma Allah ubangiji ya sa lokacin tonon asirinsu ne yayi haƙiƙa adu'ar da take ta tabbatar ba zai faɗi ba Allah sai ya bi mata hakkin cutar da ita da aka yi. Suna nan zaune sai ga Ameer da Ryan sun dawo ya sauya kaya zuwa riga da wando english wears hannunsu rike da ledoji manya da alama ba gida ya je ba, ya dubi mai martaba. "Abieey ya kamata duk ku je ku huta da safe Ammie sai ta dawo" Sun amince don a yadda yake sun san ko me zai faru ba zai amince wani ya kwanan mishi da mata ba don haka bayan Ameer ya miƙa mishi ledar suka yi sallama har Abieey ya juya Ryan ya ce "Abieey" Sai ya juyo "Abieyy ina so ka min wani alƙawari guda ɗaya" Kai ya gyaɗa "Abeey ka min alkawarin duk wani mai hannu a matsalar da Afeefah ta shiga zai biya kwatankwacin wahalar da ta sha kuma ba zaka hana ni yanke hukunci akan hakan ba! Idan kuwa har link ɗin wannan laifi ya haɗu da na mahaifiyata wanda yayi sanadiyar nesanta ni da ku gabaɗaya....." Sai ya danne haƙorinshi da ƙarfin gaske yana dunkule hannu alamar bai ma san me zai iya aikatawa ba. Numfashi mai martaba ya sauke "In shaa Allahu za'a yi duk abin da ya kamata ai wanda ya kashe mutum ba shi da sauran alfarma, amma yanzu ka yi focusing kan lafiyarta tukun" Juyawa kawai yayi ya nufi ɗakin don ya faɗa ne ma kar mai martaba yayi yunkurin hana shi daukar mataki idan har abinda yake zargi ne. Wuraren karfe ɗaya na dare ta farka, yana zaune hannunshi ɗaya a cikin nata idanunshi zube a kanta ta buɗe idanu, ta lumshe ta sake buɗewa a hankali yace "Boɗɗi kin tashi? Sannu!" Ta lumshe ido alamun amsawa duk jikinta ba kwari a hankali tace "Me ya same ni? Cikina bai taba irin wannan ciwo ba na ɗauka mutuwa zan yi Ya Saraki..." Goshinta yayi pecking ya ɗago yana shafa kanta yace "Ba yanzu ba Afeefah, ba za ki mutu ki bar ni ba" Za tayi magana sai ga Dr da wasu nurses sun shigo, bai motsa ba har suka iso kanta likitan yayi ta mata tambayoyi tana amsawa kan nurses ɗin suka dibi jininta suka mishi sai da safe suka fice. Tsabar kyaun asibitin da tsarin shi ba zaka ce ɗakin asibit suke ba don ya fi yanayi da ɗakin Hotel ɗaukar ta yayi gabadayanta yaje ya mata wanka suka dawo ɗakin, tea ya hada mata ya hau gadon yana bata a hankali har ta ce ya isheta ta sha wasu magunguna kan ya dube ta "Gabaɗaya yau me kika ci da ban sani ba?" Tunani ta tafi amma dai ta san duk abinda ta ci a ranar shi ne ya girka, gabanta ne ya faɗi ta ɗago tana kallonshi ganin kallon da yake mata na son fahimtar yanayinta ya sa ta kasa ɓoye abin da ta so ɓoyewan muryarta na ɗan cracking tace "Na sha kindirmo a sashen Mam..." "Afeefah Ban gargaɗeki akan cin komai a gidan chan ba?" Calmly yayi maganan trying really Hard to control his self sanin ita karan kanta ta jiggata amma tana fara cewa "Ka yi haƙuri maganganunta ne suka...." "To hell with the maganganun Afeefahhh" Ya katse ta da wani irin tsawa. "Raina ni kika yi ko kin dauka ban san me nake ba ne da zan ce kar ki yi abu kiyi? Kin fini sanin me nake yi ne? Ke ga ki mai sanyin zuciya ko? Toh sai ki zuba ruwa a ƙasa ki sha tunda kin yiwa kanki asarar ɗan da ko sanin zamanshi ba mu yi ba, kuma kar ki zaci alhakin akan waenda suka aikata hakan ne har ke tunda na gargaɗeki..." A razane take kallonshi bata san hawaye sun fara cika idanunta ba sai zubowar su taji ta kai hannu ta dafa cikinta muryarta na rawa sossai ta ce "Ɓ..ɓari na yi?" Ganin yayi shiru ta sake cewa "Da gaske ɓari na yi Yaya? Wlh ban sani ba! Ban san akwai shi ba da ban sha ba, kawai kindirmon ya...ya ba ni sha..." "Kin yi min shiru ko sai na tsinka miki mari Afeefah???" Baya ta matsa don yadda ya harzuko ɗin nan duka ne kawai ya saura bai kai mata ba jikinta sai ya fara rawa, kuka take yi sossai ya cigaba da masifa cike da bacin rai "Ban gaya miki duk abinda kika ji ya baki sha'awa ki sanar da ni ko menene ko a ina ne zan samo miki ba? Ko ban faɗa miki ba??? Amma da yake kunnen ƙashi ne da ke ga abin da kika janyo...." Cikin kuka da rashin madafa take furta "Am sorry...! Ka yi haƙuri na yi kuskure... Ban sani ba ne.." Bai tanka ba sai ficewa da yayi daga ɗakin gabaɗaya don ya cigaba da tsayuwa ma karya mishi zuciya zata yi. Kuka ta fashe dashi tana ambaton sunan Allah, wato ana cewa gidan sarauta na da kunne ashe ba kunne ba kadai har da ido? Cikin da ko su iyayen basu sani ba wasu sun hanga har sun cutar musu da shi? Laifinta ne wlh laifinta ne ta yi kuka har baccin wahala ya ɗauketa tunda a magungunan akwai na saka bacci bata ga Shigowar shi ba, shi ko yana zaune a reception ya jingina bayanshi kanshi a jikin gini kafafunshi a harde yana saƙe saƙe don abin nan ba zai taɓa tashi a banza ba. Washegari ko da Afeefah ta farka bata ganshi asibitin ba sai su Ammie Aisha da Adda Abeeha da kuma wasu hadimai, yanayinta duk ba daaɗi suka raka ta bayi suka fito tayi wanka suka taimaka mata ta shirya kan suka zuba mata abin kari bata da wani apetite in ta tuna haukan da tayi sai taji hawaye na zubo mata, Ammi ce tayi ta bata baki dai har take jin zuciyarta yayi sanyi. Abin mamaki ta ƙara kwana biyu a kwance har wankin cikin aka yi Ryan bai dawo asibitin ba ko ma ya dawo bata sani ba don idanunta dai basu ganshi ba hakan ke nuni da cewa ba fushin wasa yayi ba, dare haka zata yi kukanta har tayi bacci da safe ayi ta tambayar me ya samu fuskarta tace babu komai a kwana na uku aka sallame ta suka dawo masarautan kai tsaye sashenta suka kaita nan ma baya nan. Wata elderly woman Ammi ta turo tana kula da ita musamman cimarta don tana bukatar abubuwan da za su dawo mata da kuzari da kuma karfin jiki, ita dai duk abin da ta bata ci take kuma tana kiyaye dokokin matar tunda har Ammi ta ce mata da sanin Ryan ta turo matar sai bata ɗaga hankali ba, Dakon dawowanshi tayi tayi a daren sai dai abin mamaki har wurin ƙarfe 1 na dare ya shigo sashen ɗan kallonta yayi ya ɗauke kai tana sanye da riga da zani sai ɗan kwalin da tayi simple dauri da ya bayyana gashinta ta baya bayan dan kunne babu wani accesories da ta tula, bata ji sallamar shi ba kenan ciki ciki yayi abin shi ganin zai wuce ta miƙe tsaye "Ya Saraki...!" Chak ya tsaya, ta tako a hankali ta dawo bayanshi muryarta na rawa ta ce "Don Allah ka yi haƙuri, ba zan iya cigaba da jurar fushinka ba. Ka gafarceni na san na yi kuskure don Allah ka yafe min" Idanunshi ya runtse na seconds kan ya buɗe ya cigaba da tafiya bai ce mata komai ba, bayanshi ta bi tana kuka mai sautin dugunzuma hankali, share ta yayi ya cire kayanshi tsaf ya ɗaura towel ya shige bayi yayi wanka yana fitowa ya ganta tsaye again har lokacin bata bar kukan ba, zuciyarshi ne ya karye yana jin kukan har cikin kanshi. Gaban mirror yaje yana goge jikinshi da ƙaramin towel ya ɗauki bodyspray ya feshe kirjinshi dake bayyane dashi yana ƙoƙarin Juyowa kenan yaji ta kwanta a bayanshi ta saka hannayenta a kugunshi tana kuka still har hawayenta na ɗiga a fatar bayanshi, kasa controlling kanshi yayi ya juyo gabaɗaya ya bata kyakyawar runguma. "Kayi haƙuri ba zan sake kuskuren tsallake maganarka ba, fushinka na sake ɗaga min hankali don Allah ka y...." Fuskarta kawai ta ji ya ɗago ya haɗe lips ɗinsu yana bata sumba mai zurfi baya baya yake yi da ita har jikin gini, ta sanya hannayenta biyu ta zagaye wuyanshi tana bashi support, sai da ya gaji don kanshi ya raba bakin nasu suna jan numfashi a hankali hankali ya haɗe goshinta da nashi yayi pecking lips ɗin still don baya taɓa gajiya da su a hankali yace "Kar na ƙara ganin kin zubar da hawayenki wanda kika yi a baya sun isa, Allahn da ya bamu ba tare da sani ko shawarar mu ba zai bamu wani. Mu sa a ran mu haka ya kaddara wannan ɗin ba mai zuwa ba ne" Kai ta gyaɗa mishi ya ja ta bakin gadon ya taya ta cire kayanta tas ya ɗaura mata towel don su sun fi gane kwana a haka, ya ja ta suka kwanta hannunshi na yawo jikinta cike da kulawa a haka suka yi bacci dukkansu kowa da abinda yake saƙawa. Washegari da safe kan ma su tashi An shirya musu abinci wanda daga sashen Ammie ne, kuma ta yi mamakin ganin ya zauna suka ci tare don duk zamanta a asibiti Ammi ke mishi girki da kanta, bayan sun gama suka fito a tare gaisuwa yana sanye da wani Beige yard mai taushi da kyaun shi ya bayyana tsurar tsadarshi tana sanye da straight skirt and blouse da aka yi rigar da wani yadi mai sulɓi green za ka zaci fitted gown ne mai combination da lace idan baka sani ba saboda yadda ya zauna mata, alkyabbarta mai kauri ne hakan ya sa bata damu ba kuma akwai gyale Kasar shi hannunshi na riƙe da nata suka nufi sashen na Ammi, sai mamaki take da tunanin yaushe suka shirya kuma? Amma a gefe ɗaya farin ciki ne ya cika mata zuciya da har ta kasa boyewa sai murmushi take zabgawa yana kallonta bai ce komai ba har suka shiga. Sun samu Ammi zaune cikin kujera Abeeha da Aisha na karyawa yayinda Ameer ke zaune yake jan su da hira da wasa, ganin su ya sa fuskar Ammi cika da fara'a, kai tsaye gangarta yaje ya zauna Afeefah ta samu wuri a ƙasa ta zauna tana ta murmushi Allah ya gani shiryawarsu wani abu ne mai muhimmanci a gareta da bata taɓa saka goshinta kasa ba tare da ta yi mishi adu'a ba kuma Alhamdulillah ko a yanzu waninsu zai faɗi ya mutu ta tabbatar ba za su bar abin nadama ba. Gaisuwa suka yi tana tambayarta jikinta tace da sauƙi, suka gaisa da su Abeeha yayinda duk suka gaishe shi ya amsa cike da izzarshi ta jinin sarauta don fuskar a kame take tun abin da ya faru bai wani sake ba, sun jima anan kan yace ta tashi su tafi. Babu musu ta miƙe suka fice yana riƙe da hannunta da dumbin mammakinta sai ta ga ya nufi hanyar Sashen Fulani Adama, gabanta ne ya shiga dokawa amma ganin babu fuska ya sa bata yi magana ba har suka isa. Tana zaune a parlornta ta yi zurfi cikin tunani sai ganinsu tayi ita kanta ganin Rayyan mammakinta ya kasa ɓoyuwa har bata san ta miƙe tsaye ba sai da yayi murmushi ya ce "Mama barka dai mun zo ba sanarwa dole ki ji mamaki" Yana maganan yana zama, itama komawa tayi ta zauna tana kakaro murmushi "Gaskiya kam na yi mamaki ashe baka manta hanyar sashen nan ba?" "Ɗa bai taɓa mantawa da uwa ba ai Mama, Fatan kina lafiya?" Idanunta ta kawar don wallahi kallon da ta ga yana mata a take ya saukar mata da wani irin faɗuwar gaba har tana jin zufa na keto mata amma ta dake. "Lafiya Ƙalau, ashe kuma abin da ya faru kenan? Allah ya mayar da alkhairi" Afeefah da itama karon na biyu bayan zarah ta ji ta tsani matar ta gaisheta da kyar, ta amsa basu jima ba ya miƙe har sun nufi fita ya juyo ya sake kallonta ya saki murmushin da ya sake kaɗa mata yar hanji. Jeka ka dawo ta shiga yi hannunta da waya tana ta danna kira sai dai karo na sama da ɗari da wani abu kenan daga jiya zuwa yau bata samu Layin ba, yaraf ta koma ta zube tana dafe goshinta dake sara mata... 🖤Gureenjoh🖤 HAIHUWA DA HANJI (A True life story) Fatima Muhammad Gurin (Gureenjoh) Wattpad-Gureenjo6763 Arewabooks-Gureenjoh ADABI WRITERS ASSOCIATION *FREE BOOK* *57* *Ƙarshen Alewa...* Satin da ya biyo bayan faruwar ɓarin ba zata ce bata ji daaɗinshi ba sai dai ta kula tarin soyayyar da yake nuna mata ya ragu da kaso talatin cikin ɗari wani sa'in ma sai ta ga kaman ya koma mata asalin Rayyan ɗin shi na baya da ta sani, Dukda bai rage ta a komai ba na kulawa sai dai tana ji a jikinta har yanzu bai gama sauƙa ba wanda ita kanta in ta tuna sai ta yi kuka, ta fara lectures online kuma yana bata taimako yadda ya kamata ta ɓangaren, ta zuba idanu ta ga sun koma yadda suka faro amma ta kula shi bai san zuru ba dole ta sake shirin bashi haƙuri. Sannan a kwanakin ya kan daɗe a waje wani har ma tayi bacci bai dawo ba sai dai ta farka ta sameta kwance jikinshi, a yau ta yi niyyar sake tunkararshi ta sake bashi hakuri don bata kaunar wannan silent treatment ɗin nashi ko kaɗan, karfe goma ta fito wanka ta zauna ta ɗauki lokaci kwarai wurin sake gyare jikinta tsaf ta haɗa wani magani da wannan mata da Ammi ta turo mata take bata da madara ta sha, dama ta dafa mata goron tula ta zuba zuma shima ta sha kan taje ta fara neman abinda za ta saka, wani farin strapless lace bra mai haɗe da wando wanda ma kai tsaye zaka iya kiranshi bumshort ta saka ta ɗora rigar saman da ya bayyana duka fatar jikinta don bashi da maraba da raga. Gashinta ta gyare tsaf ta fito ta nufi kitchen, a yadda dare yayin nan ta san ko ya dawo ba sake cin komai zai yi ba sai ta haɗa fruit salad ta cika mishi madarar ruwa ta saka a frigde ta fita ta kara karfin Ac ta sake kunna turarukan wuta a duka burners dake kusurwan gidan sai da ta ba kowanne mintuna biyar taje ta kashe kamshin na fita a hankali ba tare da wani hayaƙi ba, tana shirin nufar ɗaki ta ji ya turo kofar parlorn sai ta tsaye nan tana kallonshi. Numfashinshi ne ya so barin shi na wucin gadi idanunshi manne da jikinta yana bin ta da wani irin kallo da ya sakata sakin murmushi ta nufo shi a yangace, gani yayi in ta cigaba da tafiyar kan ta iso za ta iya sumar dashi yasa ya yunkura kawai ya nufeta sai janta kawai yayi ya rungume yana sauke fuskanshi cikin wuyanta da wani irin salo ya sauke numfashin relief, ƙanƙameshi tayi kaman yadda shima yake sake riƙe ta cikin kirjinshi hannayenshi na sake matse ta. "you are driving me crazy My Love" Murmushi mai sauti tayi, ta raba hug ɗin tana sunne kai wai ita a dole kunya hakan kuma na sake tsuma shi tace "You are welcome My king, ka bar ni ina ta kewa" Ya saki murmushi "Daga yau in shaa Allah na gama barinki da kewata mu je ki taya ni wanka" Ya riƙe hannunta tace "Ba ka jin yunwa?" Yayi pecking bayan hannun nata yana sake bin jikinta da kallon dake rikitata ya furta "Ke kaɗai nake buƙata a yanzu idan na sameki na ƙoshi" Tayi murmushi a kunyace ta bi bayanshi zuwa ɗaki, a tsakiyar ɗakin ta tsaya chak ya waigo ya kalleta "Menene?" "Na tuna! ba fushi kake yi da ni ba har yanzu...Na baka haƙuri na baka haƙuri amma ka ƙi ka haƙura" Da wani irin salon Shagwaɓa da sanyi tayi maganan, ya lumshe ido yarinyar tana shirin zauta shi a tsaye da sauri ya buɗe idon jin motsinta sai ya ga ta juya zata fita da hanzari ya saka hannunshi ta cikinta ya dawo da ita baya har kan kirjinshi bayanta ya sauƙa ya sauƙe kanshi cikin wuyanta yana bata wet kisses da suka sa ta fara kunnuwa don ya mugun sanin weak point ɗinta yace "wa ya ce ban haƙura ba Boɗɗi? Ai na haƙura..." A cikin kunnenta yayi maganan chan ƙasa muryarshi na sarkewa. Ba zai iya jurewa har yayi wanka ba hakan yasa ya chusa hannunshi cikin yare yaren rigar yana shafa duk inda hannunshi ya sauka a fatarta har lokacin kuma yana wasa da wuyanta da harshenshi. Cikin whisper yake jefa mata magana a cikin kunne bata ma jin me yake cewa don yadda ya rikice haka ya rikitata abinda ta iya tsinta shine "lets make another baby my Queen..." Kai ta gyaɗa ya zura harshen cikin kunnenta daga haka basu ma san sun isa gado ba, sossai yayi kewanta rabon da ya ji shi a gajimare tun kan tayi ɓari sai ya ji kaman an sauya ta ne, kaman an kara mata zuma ta haukatashi ta gigitashi a duniyarta sai gashi yana sambatun da bai ma san abinda yake cewa ba ta bashi gudumawa sossai don itama ta yi kewar shi ƙwarai basu sarara ba sai da ya tabbatar bayan ya samu natsuwa itama ta samu ya rungumeta cikin kirjinshi yana sanya mata albarka. Ta sake shige wa jikin nashi tana murmushin kunya, chadak ya ɗauketa suka je suka yi wanka suka fito cikinta ta shafa "Yunwa nake ji" "Afuwan duk na yashe abincin, bari na samo miki wani abu" Ya faɗa yana kokarin saketa ta riƙe hannunshi "Just sit bari na ɗauko mana fruit salad da na haɗa ɗazu" Kai ya gyaɗa ta fice chan ta dawo da bowl mai girma dauke da spoon ciki, hannu ya miƙa mata ta bashi ya ajiye bedside kan ya janyo hannunta ta zauna kan kafafunshi bayanshi jingine da jikin gado ya shiga bata a baki sai da ta ɗauke kai ya mayar da spoon ɗin ta ɗauka ta dibo tace "Haaa" Murmushi ya saki ya buɗe bakin ta shiga bashi sai da ta kai spoon na ƙarshe ya kai hannu ya sauƙe towel ɗinta daga sama ɗan tsorata da tayi ya sa ta ɓata mishi lips sai ta Shagwaɓe fuska yayi murmushi, ta juyo gabaɗaya ta raba kafafunta tsakanin nashi tace "oops lemme help clean your mouth" Lumshe ido yayi ta kai bakinta ta sude madarar tas za ta janye yace bata isa ba nan suka sake fara ƙoƙarin komawa ruwa ita ta janye tana dariya. "Ke ko?" "Me na yi? Ba kai ne ka ja na ɓata maka bakin ba kuma daga taimako sai sai a nemi zarcewa" Ya janyota ta dawo jikinshi yana murmushi tace "Yau saura sati ɗaya aurenka ko?" A ɗan sanyaye tayi maganan, yayi pecking goshinta yana kallon idanunta yace "Ai ina da aure ni" Tayi murmushi "Ba nawa auren ba ina magana kan amaryar ka Zarah "Wace hakan?" Ta ɗan Harare shi da fararen idanunta da ya saka shi sakin kyakyawar murmushi tace "Ka fa san wacce nake nufi ko baka san sunanta ba?" "What name? Afeefahhh ita kaɗai na sani, Afeefah kamal Its the only name i learned nd i call.." Yayi maganan yana lakace hancinta idanunshi na tabbatar mata da sunanta kaɗai shi ya sani a duniyarshi. Za Ta sake magana ya haɗe bakinsu sai da ya tabbatar ta manta da maganan wata zarah kan ya zare bakin yana rungume da ita suka yi bacci cikin natsuwa da tarin ƙauna. Washegari da safe shi yayi mata breakfast don da asuba ma bai barta ba duk jikinta ya mata laushi, bayan ta karya yayi wanka ya shirya cikin wasu fararen kaya da suka amshe shi ƙwarai da gaske ga mamakin ta ta ga ya ɗauko wani alkyabba silver ya saka da yayi mugun yi mishi kyau, baki ta saki tana kallonshi sai ya ɗauko wani takalmi shima silver da ya fi yanayi da na saurata ya saka ya saka hula kan ya zauna ya naɗa rawani. "Tabarakallah Masha Allah!" Ta ambata tana sauƙe numfashi idan ba Allah ba waye? Waye ya isa kera irin wannan jarumi, santalale kuma kyakyawar namiji haka mai zati da kwarjini? Bayan nan kuma ya ɗauka ya bata matsayin miji! Alhamdulillah ta sake ambata bata san ya iso ba sai hura mata iska da ta ji yayi a fuska ta lumshe idanu tana sake buɗewa a kanshi hannu ta ɗaga a dunkule ta shiga furta mishi kirari. "Ado da kanshi ya sara maka ɗawisu...Barden maza in ka fito yaƙi ya kare, mari babban kifi maganin hadamammu...bangon duniya sun yi iya yinsu sun kasa Huda ka, Allah ya bar mini kai jarumin jarumaina...! Mai sarauta da halin girma. Tauraron sarakai jigon Afeefah Saraki kai gaba kai musu nisa kamo ka sam sam ba su iyawa sarakai duk suna a bayan ka..! Allah ya ja da zamanin Ciroman duk duniya Yariman matasan Fombina...kare ka angon Afeefah" Sossai yake murmushin da ya sake tafiya da ita ya duƙa yayi pecking goshinta yace "Duka wannan kirari nawa ni kaɗai Matar masu sarauta?" "Duk kirarin da zan ma ka wuce nan Sarakina! Allah ya bar mini kai har aljannah" Ya shafa fuskarta yana kallonta har lokacin cikin towel take ya shafa idanunta da suka sake haske da sheki zuwa lips ɗinta da ya mayar da su cherry Red tsabar yadda ya fitine su ya furta "Zan fita, ki kula min da kanki har zuwa dawowata kar kuma ki manta da cewa Saraki na ƙaunar ki... Your eyes, your voice, your smile kai komai da komai i just love everything about you" Ta sauƙo tana gyara towel ɗin ta ɗauko turare ta sake fesa mishi tana murmushi tace "I love you more takecare, sai ka dawo" Kaman kar ya tafi haka ya fice ta koma ta zauna tana murmushi. Yana fita kai tsaye Fada yayi fuskarshi a haɗe ya shiga dogarai suka fara mishi kirarin isowa, karon farko da ya zo fadan tun naɗinshi shi karan kanshi Abeey ya ji mamakin ganinshi haka, a gaban mai martaba ya duƙa "Barka da safiya Your majesty..." Sarkin dogarai zai amsa sarki ya ɗaga mishi hannu "Barka dai Ciroma, ina Fatan lafiya don da ganinka akwai magana fal a bakinka" "kwarai kuwa Adalin sarki, na zo ne zuwa na musamman a yau... Na zo ne in shigar da ƙara ina kuma fata wannan sarki mai adalci zai yi mana hukunci daidai da tsarin addini bisa adalci irin nashi" Gaban mai martaba ne ya faɗi, ya riga ya san binciken da Sameer ke yi amma baya so ko ma menene a kawo shi gaban fada shi kuma Saraki Yana so ne duniya ta shaida ta yadda kunyar duniya da mutanen cikinsa kaɗai ya ishe su kan su gamu da na lahira, yana sane yayi hakan kar ma Mai martaba yayi tunanin Afuwa saboda zumunci ko wani abu... "Na zo ne in shigar da ƙarar Makama, Madaki da Fulani Adama bisa laifin zamba cikin aminci, yaudarar masarauta, cin amana, zalunci da kuma kisan kai... Sun cutar da wannan masarauta kuma sun cutar da sarki tsawon shekaru a yanzu kuma sun cutar da abinda bai kamata su cutar ba... A Yanzu kan shari'a tayi nisa nake shaida cewa na yanke alkawarin aure dake tsakaninmu da zuri'arsu don zuri'arsu basu da nagartar amsa sunan sarauta har abada" Kallon kallo aka shiga yi cike da dumbin mamaki yayinda Makama da Madaki zufa ya shiga yi musu wanka, gabansu ke faɗuwa amma Makama ya dake ya ce "Wani irin zance kake yi Ciroma? Kar fa ka manta waenda kake zargi da waennan muggan ayyukan ba tsaranka bane kuma iyaye muke a gareka... Daga dawowarka zuwa yanzu har ka isa shiga lamuran da baka sani ba? Ka kiyaye don ba za mu yafe sharri ba ko daga waye kuwa.." Yayi murmushi ya ce "Sanin kun taka matsayin iyayen nawa shi yasa na kawo zancen inda za'a yanke hukunci da wasu ne chan. Hmmmm...." Mai martaba ya katse shi "Mecece hujjarka na wannan zargi Ciroma?" "Ina da tarin hujjoji amma kan nan ina so a gurfanar da Fulani Adama gaban fada a kuma gayyaci duka matan Laamiɗo don duk ya shafe su" Sarkin gida Mai martaba ya kalla tuni ya fice, duk fadan ana zaune shiru kowa da abin da yake saƙawa yayinda su Makama ke zare idanu suna kuma haɗa gumi da tsoron abinda wannan karamin alhakin zai iya yi musu. "Kaman yadda kuka sani gabaɗaya bana ɗaga kafa a zalunci kuma ko wanene muddin na same shi da zalunci na kan hukunta shi ne daidai da laifin da ya aikata ban cire kowa ba, Ciroma ya shigar da karar Makama, Madaki da kuma Fulani Adama bisa zargin cutar da iyayenshi da matar shi za mu so jin hujjojinshi don yin hukunci daidai da laifukansu idan kuma muka same shi da son bata suna ko wasa da hankalin wannan fada shima za mu yanke mishi hukunci daidai da laifinshi. Muna sauraronka Ciroma" Gaabɗo ya kalla sai ya miƙe da sauri ya fita, idanu Fulani Adama ta zuba mishi tana jin wani irin tashin hankali na rufe ta, da alama kallon biri take yi mishi shi kuma yana mata kallon Ayaba, a zaton ta ta toshe duk wani hanyar da zai iya sunce mata zani a kasuwa sai ya ke kokarin nuna mata shi ɗin mai zamani ne dole ta kiyaye shi. bata gama tsurewa ba sai da ta ga wasu sojoji mata biyu sun shigo da rahane da aka chanza mata kamanni ko tsayuwa bata iya yi suka gurfanar da ita, zabura tayi sai kuma ta koma yaraf ganin An sake shigo da wani mutumi an yi mishi ɗaurin huhun goro Dukda shekarunshi, azaba duk ya ishe shi ko motsi baya iya yi mai kyau.... "Kai!!!" Rayyan ya daka wa tsohon tsawa da sauri ya zube ƙasa yana roƙon yafiya cikin kuka. "Menene alaƙarka da waenchan???" Ya ɗaga kai ya kalli su Fulani Adama ya ce "Tsawon shekaru arba'in kenan ina yi musu aiki ba na asiri bane, ina ba su wani magani ne da ya shafi lalata mahaifa, hana ɗaukar ciki da ma zubar da shi idan ya samu... Sai G...gu..ba. A gafarceni Ranka ya daɗe da farko ban so aikatawa ba suka min barazana da 'ya'yana daga baya son zuciya da kudin da suke cika min ya ja ni har na zalunci Sarkin mu mai adalci.... Don Allah a yi min aikin gafara na tuba na bi Allah na bi ku ku yafe min..." Tsaki Rayyan ya ja ya kalli Rahane "Faɗi bayanin da kika yi min..." Cikin kuka da tarin nadama marar amfani ta shiga cewa "Sunana Rahane, ni ce amintacciyar Fulani Adama tun da jimawa amma ba ni na fara yi mata wannan aiki ba mahaifiyata ce da Allah ya yiwa rasuwa, ta bani labari kan rasuwar ta irin son mulki da izza irin na fulani Adama, ta tabbatar min akan mulki babu abinda Adama ba zata yi ba, ta iya makirci kala kala kuma bata bar kowa ba har mai martaba, da fari bayan aurenta da mai martaba ta zaci zata haihu plan ɗin ta kuma tana haihuwa za ta yi sanadiyar mutuwar shi danta ya zama mai jiran gado sai Allah bai kawo haihuwar ba har ya auri Fulani Aminatou anan ta yanke hukuncin muddin bata haihu ba babu mai haihuwa a wannan masarauta har mai martaba kuwa don haka ta yanke hukuncin yin mai gabaɗaya Wai Haihuwa da hanji da taimakon yayanta da ƙaninta suka samu wannan mai maganin sadidan yake bata maganin hana ɗaukar ciki.. A kowani sashe na matan sarki tana da amintacciyar baiwa da take biyan su makudan kudi suke yi mata aikin zuba maganin nan a abinci kowace mace da mai martaba ya aura, tun Fulani Aminatou bata shekara uku ba ta gama da mahaifarta yayinda a fili take nuna tausayi da neman taimako ga mai martaba wanda hakan ya bata matsayi mai girma a idanunshi, Shigowar Fulani Faɗimatu ya zame mata barazana don bata yarda hadimai su mata girki ba kuma idan tana yi bata nisa da bakin murhunta hakan yake bata damar ɗaukar ciki tunda duk abinda ta girkawa mai martaba ma babu maganin, duk ta ɗauka Fulani Adama kan san yadda tayi ta sha wannan magani da take karɓo wa cikin ya ɓare. ko da ta samu cikin farko na yarima Aliyu ta gudu Mambila babu yadda basu yi ba su sayi hadimarta mai rasuwa Hanne ta zuba musu maganin ta ƙi har alkawarin kasheta suka yi amma ta ƙi amincewa bayan sun dawo masarauta suka samu nasarar ba wa yarima Aliyu guba ya ci ya mutu fahimtar za ta iya tona musu asiri itama suka yi ajalin ta. Cikin Ciroma Sameer ne ya zo musu bazata don ita kanta mahaifiyar bata san da ciki ba sai da ya girma, sun yi duk yadda za su yi sai dai Zakaran da Allah ya nufa da chara ko ana muzuru ana shaho sai yayi dole ya zo duniya, sun so kashe shi yadda suka yi wa Yarima Aliyu amma shi ɗin murucin kan dutse ne bai fita ba sai da ya shirya ya zame musu kabewar kan ƙabari bakin cikin mai taushe, daga karshe dole suka sa mahaifiyarshi ta rabu dashi ala dole don babu yadda ta iya tana so wa danta rayuwa. Fulani Adama ta fi tsanar Fulani Faɗimatu akan duka matan sarki don Cikin lokaci kankani ta lalata wa Fulani Salimah ma mahaifarta ita ce ta zame mata gagara badau bisa kariyar Allah, a farkon aikinta babu asiri babu tsubbu don duk ta fi gane kirsa da makirci amma Makama da ya fi kowa son mulkin yana ganin kaman ko ba jima Ciroma Sameer zai dawo sai ya je yayi mishi asirin da zai saka ya manta komai da kowa, ya mishi asirin da zai ji ko sunan iyayenshi ba zai iya ambata akan harshenshi ba, ya saka mishi tsanar masarauta da sarautar gabaɗaya, Kwatsam sai ga shi ya ɓullo kaman huduwar rana tafin hannu yayi kaɗan ya kare shi sun shiga tashin hankali don basu taba zato ko tsammanin bayyanuwar shi ba tunda an tabbatar wa Makama cewa asirin ba mai karyewa bane don kogi aka jefa aka ba wa tsuntsu wani ya fire sai gashi ya dawo kuma da wata mace. Anan suka yanke hukuncin aura mishi zarah da haɗin Bakinta na daga ta aure shi sarki yayi murabus za su kashe shi su kashe sarkin sai su karbi sarautar har dan Zarah ya girma, kwatsam ta fahimci Fulani Afeefah na da juna biyu, hankalinta ya tashi ta aikeni wurin mai maganinsu inda ya bani magani na kawo sai dai duk abinda aka bata bata ci har sai da Fulani ta yi mata wasu maganganu da suka raunata zuciyarta ta sha fura, a cewar mai maganin sai bayan sati ma zata yi ɓari kar ma a zarge ta tunda da wayon ta ba zata bari a lokaci ɗaya ta zubar da cikin ba dayake Allah ba azzalumin bawan shi ba akwai rabon kamatan dumu dumu bisa laifukanta sai cikin ya ɓare a ranar dole aka san me ta ci kuma a ina ta ci inda daga ranar Ciroma Sameer bai bar su sun shaki iska ba. Ya kama ni aka dinga min horo iri iri bai bar ni ba sai da na faɗi komai na kuma kaishi wurin mai maganin aka kama shi... Ku yafemin don Allah ku yafe min na tuba wallahi umarni kawai nake bi don tsira da rayuwata" Cikin kuka mai tsuma zuciya ta ƙarasa. "Innalillahi wainna ilaihi rajiun..! Innalillahi wainna ilaihi rajiun" Abinda ke tashi kenan a fadar duka matan sarki kuka suke yi mai tada hankali yayinda mai martaba ya runtse ido yana jin hawaye na sulmiyo mishi, ashe kashe mishi yaro suke niyyar yi shiyasa take kanainaye shi da kissa da komai take cusa mishi son auren Zarah da Sameer? Ya gode Allah da ba'a yi auren ba da ba zai yafe wa kanshi ba. "Wallahi na yi nadama tun ba yanzu ba amma tsoron hukuncin Fulani Adama ya sa na kasa daina basu magani, yarana sun mutu duk a gobara na auri mata sama da biyar duk suna gudu su bar ni don na kasa basu haihuwa, tun mutuwar yarana na yi nadama amma ban san yadda zan yi ba a gafarceni" Tsohon ke fada. Fulani Aminatou tace "Allah ya isa! Allah ya isa tsanina da ku duka wallahi Allah ko da ni kaɗai ce zan yafe muku ku shiga aljannah ba zan taɓa yafe wa ba" Fulani Salima ma Allah ya isa take jerawa cikin kuka mai ciwo, mai martaba hawaye kawai yake yi haka Ammi dake jin mutuwar yaronta ya dawo mata sabo. "Babu aure tsakaninka da Zarah har Abada Ciroma, ku kuma wannan kaɗai ya ishe ku tsoron Allah, wannan kaɗai ya kamata ya ishe ku ishara.... A tube musu duk wani rawanin zuri'arsu ku kuma shaida na yanke igiyar aurena da Adama a dibe su a kaisu kurkuru mafi azabtarwa na wannan masarauta kan a yanke musu hukuncinsu.... A tabbatar basu samu natsuwa ko kwanciyar hankali ba" "An gama ranka ya dade" Sarkin dogarai ya zube ya amsa kan wasu majiya karfin suka shigo suka saɓesu ko damar magana ba'a basu ba, kunya da dana sani marar amfani na rufe Adama komai ya kare mata a lokacin da bata yi tsammani ba. Rayyan ya dubi Afeefah dake kuka ya girgiza mata kai a hankali yace "Na gode Afeefah. Na gode kwarai ta sanadiyarki asirinsu ya karye idan baki manta ba duk ayoyin da kike yi wa Saleem a tare muke sha Dukda ban san da zaman wani asiri a jikina ba, Kin ba ni babban dama ta sanadiyarki na samu faɗa wa Mammi abinda ta jima tana son ji na wanene ni kafin mutuwarta. Ba zan taɓa manta wannan taimako naki ba na gode" Ammi ta rungumeta tana kuka. A haka aka watse zaman fadan mai martaba sai riƙe shi aka yi zuwa sashenshi tuni Rayyan ya maƙala mishi ruwa don ba karamin hawa jinin shi yayi ba. 🖤Gureenjoh🖤 HAIHUWA DA HANJI (A True life story) Fatima Muhammad Gurin (Gureenjoh) Wattpad-Gureenjo6763 Arewabooks-Gureenjoh ADABI WRITERS ASSOCIATION *FREE BOOK* *58* Alhamdulillah komai ya cigaba da tafiya normal bayan nan, ta cigaba da lectures ɗinta cikin kwanciyar hankali kuma tana samun duk wani kyautatawa daga zuri'ar na mijin nata kaman yadda shima yake kara samun kusanci da iyayenshi, Mai martaba ya sha jinya kan ya warke ya tara matan yayi ta basu haƙuri a ganinshi komai ya faru ne sanadin aurenshi da suka yi, sun nuna haka ƙaddarar su take sai dai Fatan Allah yayi musu sakayya akan Adama, Zarah da bata san komai ba sai da aka warware daga farko ji tayi duniyar yayi mata zafi damuwa yayi mata yawa ta tattara ta koma wurin mahaifiyarta da dukkansu har yan uwanta kunyar abinda mahaifinsu ya aikata ya sa ba sa iya ko fitowa, Ammi bata neme ta ba haka Aisha don tunda har ta yi niyyar auren Rayyan ne don ta cutar dashi su ma suka ji ba za su iya cigaba da hulda da ita ba amma Aisha tayi kuka kaman ta mutu, ta ɗauki zarah kaman 'yan biyunta ne bata zaci hakan daga gareta ba. Maganan yanke hukunci sai da suka yi wata biyu suna cikin na uku garƙame cikin azabtarwa kan aka yankewa Fulani Adama hukuncin kisa ta hanyar rataya, Makama da asirinshi ya dawo mishi ya haukace damuwarshi kawai a barshi yayi ta tafiya ji yake kaman kwakwalwarshi zai fashe idan bai shiga duniya ba dukan da yake yiwa Madaki yasa aka raba musu ɗaki, shi Madaki da sauran hadiman an yanke musu life imprisoment iyalan su sun yi kuka kaman ba gobe amma bahaushe ya ce tsuntsun da ya ja ruwa shi ruwa kan yi wa dukan tsiya. Soyayya tsakanin Saleem da Aisha yayi nisa don har ya turo mai martaba yace za su yi fixing rana sai a haɗa da na Ameer da ya kasa komawa da Abeeha dake shirin gama makaranta, Jiddah dai da tayi mugun kewan su sai dai a haɗu a yi ta waya. Yau ya kama ana ya gobe Afeefah za ta gama First semester examination ɗinta kuma Rayyan ya tabbatar mata a satin za su fara shirin tafiya Kaduna don ta matsa mishi sossai akan komawa ga su Suhail da kuma su kawu Dukda shi baƙin cikin kawun bai taɓa wankuwa mishi a rai ba sai dai bai hanata ba don haka mai lalle ta nema Ammie ta turo mata har sashenta. Tana zaune da dogon wando da wani shirt Black na ma Rayyan ɗin ne daga ganin girman da yayi mata amma ta fi jinta comfortable ciki, ta ɗaura Black dan kwali a kanta an gama lallen kafa da hannun duk an saka leda su Aisha na gefe suna ta hirar su da ta shafi rayuwa har jan ya kama aka cire mata sai aka zana mata baƙi a bayan hannun don ta ce jan kawai ya isa a kafafun yarinyar kwararriya ce kuma lallen ya mugun kamawa yayi maroon sharrr kaman ka sace kafafun in ka gani, Rayyan ne yayi sallama ya shigo duk suka mishi sannu da dawowa daidai an gama baƙin kenan ya tsaya yana kallon hannun kan ya ce "Wai tunda na bar ku kina nan wurin zaune?" Ta karkata kai fuska a ɗan Shagwaɓe tace "Kwalliyar kenan sai wahala duk yunwa ma nake ji babu hannun cin" Ya kalli hannun nata sai ya nufi kitchen, Aisha da Abeeha suka kwashe da dariya suna tafawa "Sai da ke Matar mijinta" Aisha ta faɗa tana dariya. Abeeha tace "Ku tashi mu tafi yanzu bai wuci abinda zata ci ya je nema mata ba kan ya dawo ya kora mu ko su makanta mu gwara mun yi ta kanmu salin alin" Afeefah na ce musu su tsaya ko ta kanta basu bi ba suka tarkata suka tafi sai gashi ya dawo hannunshi rike da wani plate. "Duk ka kora min 'yan hirar Ya Saraki..." "Dama wani amfani suke dashi a gareki idan ina nan? Babu so Haaa ki ci abinci" Murmushi ta saki tana bude baki ya saka mata Nan-bread guda biyu da ya sanyo a plate ɗin da curry chicken da ya zuba a gefe, da hannunshi yake bata yana tabbatar da bai ɓata mata jiki ba har ta ƙoshi ya bata ruwa ta sha kan ya shiga duba lallen. "Kin yi wa lallen nan kyau ainun Boɗɗi na" Tayi murmushi tana sake kallon lallen "Ko kuma shi ya min kyau dai ko Ya Saraki?". "Wai dama baki sani ba?" "Mene?" "Ado biyayya yake miki, Kwalliyar da kanshi ke kike mishi kyau ba shi yake miki kyau ba.." She's just blushing don bata gajiya da sauraron dadadan kalamanshi yana ɗan wuya ya sake bakin don haka idan ya sake yana zubowar tana amfani da damar ta adana a cikin zuciyarta ta yadda ko baya nan in ta tuna fuskarta kan zama ya cika da tarin murmushi. Washegari kuwa aka kai ta paper yadda aka saba motoci biyu har gaban exams hall su jira ta gama a dawo da ita gida, yau ko da ta fito bata gansu ba, daga jikin hall ɗin ta tsaya sai ta ga call nashi tayi picking ya ce mata ta taho yana kallonta fuskarta cike da fara'a ta nufi motar nashi don a yau da kanshi ya zo ɗaukar ta. Idanunshi da ya zura mata tun tahowarta ya lumshe a sadda ta yi masauki gaban motar kamshinta mai sanyi da natsuwa na ratsa shi "Hey Assalamu Alaikum" Ta furta a hankali tare da miƙa mishi hannunta ya ɗan murmusa kan ya miƙa nashi ya shigar cikin nata yana kallon tsakiyar idanunta ya furta "Wa'alaikissalam warahmatullah" Cire hannunta ta so yi sai ya gimtse yana mata kallon baki isa ba kuma ai dariya ta ɗan yi, ya miƙa hannu gefenshi ya zaro wani rose Red nd green dake fidda sassanyar kamshi ya miƙa mata. Da hannu ɗaya ta karɓa ta kai hancinta tana lumshe ido fuskanta ɗauke da murmushi tace "and this?" "I am bribing you a ban dama in fitar dake outing” Dariya ne ya ɗan kufce mata "seriously? Ai na zaci saurayi da buduruwa ne ke fita date ba mata da miji ba" Tayi tambayar tana wara fararen idanunta a kanshi ya kai hannunshi ɗaya kan kumatunta ya shafa "Babu laifi a hakan.... Afeefah ki na da kyau fiye da duk wani abu mai kyau, kina da daraja fiye da duk wani abu mai daraja a kullum soyayyarki ƙara yawa take a zuciyar Ryan, I will always love you again and again...kullum sabunta kanshi soyayyar ki ke yi so i have to be very caution" Tayi murmushi mai cike da tarin alfahari tana sake shinshuna kyawawar furen dake hannunta. Motar ya ja suka fice daga makarantar. "Kin ce za ki yi sayayyar su Suhail should we start with the shopping ko mu je ki sha ice cream?" Tayi murmushi tana sake jin alfahari zuciyarta fal godiyar Allah tace "Lets start with the shopping" Kai tsaye shopping din ya kaita a tare suke tafiya hannunshi rike da nata ɗayan yana tura chart na shopping din ita kuma tana duba abinda zata ɗauka. Tsaye yake sai dai bayanshi a jingine da stall ɗin kayayyaki inda suke babu wasu yawaitar mutane, ita ke sayayya shi ya zuba mata idanu yana aikin kallo, sanye yake da full Black Jean nd top ya saka facing cap da ya zauna mishi sossai saboda mutane kar su gane shi, takalman kafafunshi ma bakake ne, hannayenshi duka a zube a aljihu... Don tun dazu suke tsaye wurin choculates ɗin tana ta rawan ido. Ta ɗauko wani choculates tana dubawa sai kuma ta ɗan ɗago karab suka haɗa idanu kusan karo na biyar kenan a take ta Shagwaɓe fuska tana kallonshi ya ɗan saki smile yana ɗage mata gira guda "ya dai? Na miki ne?" Ya ƙarshe da wani kayataccen murmushi... "Ni ya kamata in ce haka ai tun da ni ake ƙarewa kallo.. Ni Allah watarana har muni na sai ka binciko" Ta faɗa cikin yanayin da ya saka shi faɗaɗa murmushin shi, choculates na hannunta ta ɗaga sama "Ina son picking wa su suhail wannan yayi ko? Ko me kake tunani?" Very naughty yana ɗan lashe lip ɗin shi na ƙasa ya furta "I am thinking of kissing you..." Hannu ta saka ta rufe baki tana zazzaro ido ya saki dariya mai sauti kan ya yunkura ya nufe ta, kalle kalle ta fara kan ta yunkura kuwa da gaske yayi pecking lips ɗin nata hannunshi na ɗan manna ta da jikinshi. "Ya Saraki waje fa muke" "Ina ruwana" Ganin yana ta kallon fuskarta ta san zai iya aikata abinda ma ya fi haka don haka ta janye ta saka choculates ɗin tace su tafi ita kam ta gama, sai murmushi yake mata don ta bashi dariya yadda take zare ido kaman yayi komai ne gaban mutanen, shi ya biya kuɗin suka fice. Sossai suka zazzaga ya kashe ta da tarin soyayya wai murnar kamallah exams sai dare suka koma masarautan, a sayayyanta har su Ammie ta yiwa don haka tana idar da isha ta fito hadimarta tayi saurin karbar manyan ledojin hannunta suka nufi sashen Ammin don shi bai shigo ba tukuna, ta shiga sashen Ammin da sallama sai idanunta suka sauƙa kan zarah dake tsugune ƙasa sanye da hijabi tana kuka sossai. Gefe ta samu ta zauna bata ce komai ba har zarahn ta gaji da kukan ta fara roƙon su yafiya duk ta rame tayi duhu. Ammi ta sauke numfashi tace "Zarah ki daina kukan nan haka ni kam na yafe miki, wlh ban taɓa bambanta ki da Aisha ba Dukda na ji mamakin ƙudirinki a kaina amma tunda kin gane kuskuren ki Allah ubangiji ya yafe mana gabaɗaya" Aisha ma tace ai ya wuce. Ta kalli Afeefah zata yi magana Afeefah tace "Ni dai baki min komai ba wlh zarah. Allah ubangiji ya cigaba da ɗora mu duka bisa turban gaskiya" Suka amsa da Ameen kan ta miƙe ta fice suka bi ta da kallo. Afeefah ta gaishe da Ammie ta amsa cike da kulawa tana tambayarta exams "Alhamdulillah Ammie mun gama lafiya" "Allah ya ba da sakamako na alkhairi, yanzu sai shirye shiryen tafiya Kaduna ko?" Kai ta gyaɗa Ammie tace "Masha Allah, Allah ya nuna mana. Akwai saƙo zuwa da safe za'a kawo miki sai ki duba ki ga idan akwai abinda kike son ƙari ko chanji duk sai a yi" Godiya tayi sossai kan ta miƙawa Ammie ledar hannunta daidai Rayyan ya shigo kenan tana cewa "Ammi mun je shopping ne sai na ɗauka muku da Abeey" Ta miƙawa Aisha nasu. Ammie ta buɗe ledar Dukda duk wani kyauta da za'a yi mata tana da halin yin fiye dashi amma kyautatawa abu ne mai daaɗi kwarai kuma ta ji daaɗi har ƙasan ranta Leshi ne mai tsadar gaske sai turare shima designer na Abeey, Abeeha da Zarah dogayen riguna ne egypt Abaya sai yan abun ciye ciye tarin choculates. Shi karan kanshi Rayyan fuskanshi ya nuna jin daaɗi ainun Dukda tare suka Saya amma ko kusa bai san har da su Ammie ta yi wa sayayyar ba sai darajar ta ya ƙaru a idanunshi barin ma da ya ji adu'o'in da Ammie ke yi mata anan ya fahimci duk kudin iyaye kyautata musu na saka su farin ciki kuma hakan Allah ne kadai ya san irin ladar da zai baka bisa wannan murmushi da ka sanya su aiko ya ƙudiri aniyar cigaba da ganin wannan murmushi na Ammie, Sai kusan goma suka bar sashen. Bayan kwana biyu da gama exams ɗinta suka fito a shirye tsaff cikin shiga na alfarma, tafiyar har da Abeeha da Aisha don duk sun gama exams motoci shida ne ya kaisu Airport yana riƙe da hannunta cike da kulawa da so da kauna har suka sauƙa a filin tashi da saukar jirgi na Abuja, anan ma motocin alfarma bakaken prado sai sheki suke da securities ne suka zo ɗaukar su ya san aikin mai martaba ne don haka babu wani dogon nazari suka shiga zuwa gida, sun samu gidan a cike su Saleem da sisters ɗin shi ga Sulaiman da matarshi da Twins su fauza ga jidda an shirya musu abinciccika iri daban daban kasancewar tafiyar mintuna 40 ne ba wani gajiya suka yi ba nan Sulaiman da Saleem da kuma Rayyan suka zauna sitting room yayinda 'yan matan suke ta hira a parlor babu wani nuna bakunta ko rashin sanayya kaman 'yan uwa. Sai wuraren isha duk bakin suka tafi Aisha ta sauƙa ɗakin Afeefah na ɓangaren Mammi yayinda su Afeefah suka sauƙa sashensu. Washegari da safe suka fito a shirye tsaff suka shiga wannan motocin nan a jere suka Lula sai Anchau Shigowar su Layin su Aunty zee suka jera gabaɗaya securities ɗin suka fiffito aka buɗe musu kofa za ta sauƙa ya riƙe hannunta yana kallon gidan da ya fara ganinta ciki a sadda ta sallamar da Rayuwa, ita kanta tana tuna ranar da aka yi yunkurin kashe ta a wannan gida, tana tuna rayuwarsu da Aunty zee tana iya tuna ranar da ya fara tare ta a cikin jikinshi lokacin da ta yanke yin mai Dungurun gum da rayuwarta Wai HAIHUWA DA HANJI a sadda ta sallamar cewa barin ta duniyar shine maslaharta idan har ta tafi ai shikenan babu mai kallonta bare yayi mata sharrin maita ko zama annoba. Idanunta cike da hawaye ta kalleshi ya lumshe nashi cikin su fuskarshi babu walwala yace "Kin ga dalilin da ya sa bana so ki zo ko?" Ta mayar da kanta ƙasa ta san kuka kam sai ta yi shi kuma abinda baya so kenan sam. "Ki min alkawari ba za ki yi kuka ba" Tayi shiru bata ce komai ba, ya zame hannunshi yana sauke numfashi sai ta juya ta sauƙa ta nufi kofar kyauren gidan da ya tsufa mata ainun kaman ba gidan Aunty zee ba da yake fes fes, jama'ar unguwa dayawa sun fita suna kallon wanda ya zo don jiniyar masu take musu baya ya ja hankalinsu sossai. Sanye take da wani dakakken purple lace mai shegen tsada an yi mata dinkin Borno style straight skirt da bubu da yayi mugun kyau ta zuba accesories gold ne daga wuyanta zuwa hannunta mayafinta ya zauna mata sossai hannunta rike da wani sabon designer bag da ta dauka cikin kayan aurenta da har lokacin suke gidansu na Kaduna don bata tattare ba, sai takalmin ta mai ɗan tudu wannan vibe ɗin na manyan mata kuma hajiyoyi yan gatan mazajensu shi take bayarwa har ta tura kofan gidan ta sanya kai da sallama. Wasu yara biyu ta gani suna wasa sanye da wasu kaya da suka fi yanayi da tsumma sun yi dukun dukun macen gashinta kaman wanda yayi shekara bai ga ruwa ba, kafafunsu babu takalmi, ganin ta yasa suka tsaya suna kallonta kamannin fuskokin su yasa taji tayi bursting to tears, gabanta na tsananin faɗuwa ta ce "Suhail...! Suhailaah???". Abeeha ce ta dafa ta ganin tana ƙoƙarin faɗuwa saboda jirin da ta ji ya ɗauketa a lokacin da suka amsa, waennan su ne yaran Aunty zee? Su Suhail ne haka? Innalillahi wainna ilaihi rajiun "Ina Babanku?" Cikin maganansu suka ce "Yana ɗaki kwance ba shi da lafiya" Da sauri ta nufi ɗakin da yake kwancen babu komai cikin ɗakin sai tantagaryan siminti, me ya faru? Ta fara tambayar kanta kan ta isa inda yake kwance kan taburma idanunshi a buɗe yana kallonta ta duka gangarshi "Uncle Usman!!" Hawaye na zubo mata babu kakkautawa a hankali yace "Afeefah?? Ke ce??" Hannayenta ta sa ta toshe Bakinta tana sakin kuka da gaske su ɗin ne cikin wannan hali? "Uncle me ya faru? Ina Hamdiyya? Me ya samu aikinka baka da lafiya ne?" Duk ta rasa ma me zata tambaya shima yana kuka yace "Ki yafe min Afeefah don Allah ki yafe min na cutar da ke, na kasa rike amanar da zainabu ta tafi ta bar mini ki gafarceni AFEEFAH" "Baka yi min komai ba uncle wlh baka yi min komai ba hasali ma ka rike ni da amana tsawon shekara da nayi a gidan nan baka taɓa hantara ta ba, wlh baka min komai ba ni ban ga laifinka ba ko da ka zarge ni saboda ina da tambarin tun farko manne a goshina" "Na kasa amincewa da cewa Allah ne me kashewa kuma mai raya wa, hankali na ya tashi ainun don bayan mun binne zainab kin dawo mun kore ki sai muka muka je asibiti da su Suhail za'a yi musu riga kafi a kuma ba mu madarar da ya kamata su cigaba da sha anan ne likitan ya ji maganan da muke yi da Hamdiyya da maiyya ce ta kashe zainabu yayi saurin taka mana birki ya kuma shiga yi mana bayanin abinda ya faru da zainabu wanda bamu sani ba, ya ce mata dayawa suna samun wannan matsala na Postpertum ko a samu taɓuwar mu'amala ko irin ciwon cikin wasu kam ma har a zaci sun haukace ne, ciwon cikin nata bamu farga da wuri ba sai da ya mata illah kwarai muka koma a sannan babu abinda za su iya ta rasu. Hamdiyya kuma dama ta jima tana yi mata hassada tana jin haushin yadda ta samu ciki ita tana zaune hakika ta yi yunkurin illa ta cikin tun kan su zo duniya Allah na kare su har ta haihu tana ganin kaman za ku haɗu ku kwashe dan abinda na mallaka da ke da zainabu ga yarana da farin cikin samuwar su bai ɓoya mini kuma dama ta jima tana sanyawa ranta ba sonta nake ba na aureta ne kawai don in haihuwa a yanzu da bata haihu ba matata ta haihu ta gama amfani kenan zan iya sakarta kowani lokaci hakan yasa ta ƙarfafa hassadarta a kanku musamman ke tana amfani da baƙanta miki tana kuntatawa Zainabu. A ƙarshe tayi sanadin da kika bar gidan nan anan ta fara rainon azaba ga yarana ba tare da na sani ba, duka zagi tun basu san kansu ba, ta bar su da yunwa ta bar su cikin ruwan wanka duka don ba ita ta haife su ba Allah ne ke kare su ban sani ba, a ranan da na san duk abinda take kullawa na shiga masifar tashin hankali marar misaltuwa musamman in na tuna abinda na yi miki daga nan jinina ya hau na samu matsalar shanyewan jiki, a takaice Hamdiyya ta tattara komai ta sayar akan ba zata iya zama da ni ba ga jinya, ga rainon ƴaƴan da ba nata ba kuma bata da damar haihuwa, ko sati ba'a yi ba na samu labarin mota ta kaɗe ta ta rasa kafafunta ta kuma rasa rabin fuskarta duk kudin yana tafiya a jinyar da har yau bata warke ba. Kuɗin da Zainabu tayi ta ajiye miki a asusu da su na tsira sai waenda abokan arziki kan kawo da shi nake aika yaran nan su sayi abinci su ci ko makota su basu, bana iya yi musu komai ko wanka sai dai su je su watsa" Sossai Afeefah ke kuka, Allah sarki rayuwa amma Hamdiyya ta cika azzalumar matar uba kuma ko a yanzu ta ga ishara, Rayyan Aisha ta kira don Afeefah ta kasa daina kuka hankalinta ba karamin tashi yayi ba shi ya kira aka dauki uncle Usman yace a koma cikin Kaduna dashi a kaishi asibiti zai kira Sulaiman kan su juyo. Su Suhail na rungume da Afeefah suka fito zuwa mota yan unguwar na zuwa su gaisheta suna ta mamaki har wasu na tambayar ko Afeefahn Aunty zee ce ta gyaɗa musu kai, Rayyan ya zubar da dukiya don duk wanda ya nuna ya gane ta aka gaisa sai ya mishi kyauta daga nan suka nufi Dutsen-wai. "Afeefah!" Ta kalleshi ya riƙe hannunta ya sa hannu yana share mata fuska yace "kuka sam bai kamace ki ba, ko don zafin da nake ji a nan ya kamata ki sassauta" Ya ƙarasa yana nuna zuciyarshi. Ta gyaɗa kai ya ce "Na san burinki shi ne ki yi kuɗi, ba kuma don wani abu ba sai don ki tallafawa al'umma musamman na ƙauye irin cikin kauyen ku da ake rayuwa kara zube babu neman ilimi, babu sana'a ana rayuwa irin rayuwar dabobbi ko zamanin da chan baya, ina so in sanar miki cewa na ba da wannan gudumawa na buɗe miki Center na farko ina fata ya zama farkon buduwar tarin alkhairanki... Ina adu'a Allah ya sanyawa gidauniyarki daga na farko har na karshe albarka ya dafa miki ya kuma isar miki da ladan... Akwai Center da aka gama buɗewa a Dutsen-wai da Sunanki a yau za'a yi taron kaddamarwa a cikin wannan plaza akwai kayan aiki da malamai na Musamman da zasu ke koyawa mata sana'o'in dogaro da kai kaman su ɗinki da sauransu akwai kuma makaranta islamiyya da malaman da muka yi hiring na musulunci da za su tsaya tsayin daka wurin ganin sun koyawa matan wannan kauye da ma mazan addini akwai kuma babban masallacin juma'a a kusa da wannan plaza shi kam na Mammi ne ina Fatan duk Sallar da za'a yi ciki ladar ya isa gareta. Ba ni da alaka da kula da wurin daga yau duk naki ne ga takardun da ma komai da komai na plaza ɗin kyauta ne na musamman zuwa gareki" Jikinshi kawai ta faɗa don ta gigice ta rasa ma wani irin abu zata yi, kuka kawai ta saka mishi yana ta aikin rarrashi za tayi godiya ya manne Bakinta da nashi yana kissing passionatly sai da ya tabbatar ta daina hawayen kan ya saki yayi pecking goshinta "Anything for you my baby girl ki sani wannan ɗin mafarin nasararki kenan a rayuwa, duk wanda ya baƙanta miki a da a yanzu yana a karkashin kafafunki, na ji daaɗi da kika nufi saka musu da alkhairi bayan sun bi ki da sharri amma ki sani wannan yunkuri naki na basu ilimi makami ne mai girman gaske a duniyarsu ladar ki sai a wurin ubangiji" Daidai nan suka isa cikin Dutsen-wai ita ke kwatanta musu har kofan Gidan Kawu Labaran. 🖤Gureenjoh🖤 HAIHUWA DA HANJI (A True life story) Fatima Muhammad Gurin (Gureenjoh) Wattpad-Gureenjo6763 Arewabooks-Gureenjoh ADABI WRITERS ASSOCIATION *FREE BOOK* "Last Page na zuwa anjima in shaa Allah. Wlh jiya na yi gajiyar da ban san adadi ba ina buɗe ido da niyyar typing idon na rufuwa ganin ba zan iya ba yasa nayi bacci and yau ma same thing zan lallaɓa in ba ku shafin karshe in shaa Allah. Na gode da haƙuri da ni* *59* A gaban gidan ta tsaya ta ƙura mishi idanu kaman yanzu ne komai ke faruwa da ita, tana tuna baƙar wuyar da ta ci daki-daki cikin wannan gida, hawaye ne suka cika mata idanu shaidan na raya mata ta juya ta koma kawai don basu chanchacanci duk wata alfarma daga gareta ba, da kyar ta hadiye wani abu da ya tsaya mata a wuya tana tuna ni'imomin Allah a gareta sai ta furta Alhamdulillah don ko daga fasalin gidan zaka san cewa rayuwa ya ƙara taɓarɓare musu wane wane don daga inda take tana kallon har kofofin dakunan gidan saboda rushewar ginin ƙasan dake zagaye da gidan, yunkura wa tayi zata shiga sai ta ga Fitowar wani dattijo a yanayin shiga da fuskarshi ya nuna kamilalle ne wanda kai tsaye bata kawo ko kusa Kawu Labaran bane sai da suka haɗa idanu, Chakk ya tsaya yana ƙare mata kallo kaman yadda ita ma take ƙare mishi kallo. Sanye yake da jallabiya baƙa har da hula taɓani ka ji hadisi da chasbi riƙe a hannunshi sai wani littafi da ya nuna mata na addini ne, ya rame kam gabaɗaya ya lalace, shi karan kanshi bai gane ta ba sai da yaga kallon da take mishi da hawayen dake zuba mata don kaman an yi mata wankin inji ne, kaman bata taɓa sanin menene wahala ba a rayuwarta, muryarta na rawa tace "Ka..kawu" Tana tuna ranar da ta zo da Saleem yayi mata kora irin ta miyagun aljannu da kayan tsubbu da komai. "Af...Afee..fah??? Ke ce Afeefah? Da gaske ke c..e?" Cikin wani irin karyayyen murya yake maganan, ta ɗaga kai sai gani tayi ya iso gabanta ya zube gwiwowinshi ƙasa da sauri itama ta durkusa yadda yayi suka saki kuka a tare, nata dai bata san me take ji ba don abubuwa ne suka haɗe mata shaidan na tuno mata duk wani minti da tayi a gidan cikin azabtarwa yana tuna mata irin muggan kalaman kawu a kanta da rayuwarta yana nuna mata basu chanchanci komai na alkhairi daga gareta ba ta wani ɓangaren tana jin babu daaɗin yadda ta zo ta ga inda suke rayuwa da kuma lalacewar da kawun yayi kaman kuɗin guzuri. Shi kuwa nadama ce, nadama da kunyar kasa riƙe amana da zumuncin ɗan uwanshi yake yi wa kuka, kunya mai tsanani da ba zai iya cewa ya taɓa jin irin shi ba yake ji na ɗiyar cikinshi. "Afeefah idan na ce ki yafe min na so kaina dayawa, na san na yi miki abubuwa masu yawa na zalunce ki, na ci amanar zumunci, na cutar da rayuwarki fiye da ƙima, na wargaza natsuwarki har ya kai na kore ki da kaina daga kusa na bisa tarin jahilci da baƙar zuciyata... Ina kallo matana kowacce take abinda ta so da rayuwarki ana gara ki kaman kwallo, na dauke ki da kaina na jefawa hukuma ke don kawai ina ganin kin zame min Ƙashin kifi, an zo neman aurenki har nan na lalata komai saboda kawai wani zargi wanda babu wanda ya tabbatar, saboda son zuciya irin tamu... A ƙarshe na aurar dake ba tare da na ko yi binciken wanene za ki aura ba, mecece sana'ar shi, su waye danginshi don kawai sun cika ni da kuɗi sun kuma nemi auren kawai suke so, tun bayan aurenki da kaddara ta faɗa min bisa neman zuwa wurin ki da nayi na ci arziki na faɗa hannun 'yan shan jini a ranar na san cewa ke ba Mayya ba ce yadda muke faɗa, a ranar na tabbatar harkar shan jini da maita ya fi karfin kwakwalwarki nadama mai yawa ya rufe ni a kullum Adu'a ta shi ne yadda zan ganki kafin ƙasa ya rufe min idanu Afeefah...." Sossai yake kuka ta mayar da kanta ƙasa tana cigaba da hawaye, hatta Aisha da Abeeha hawaye suke shi kuwa Rayyan kanshi ya kawar yana jin zuciyarshi na jagulewa. "Ashe za ki zo inda muke Afeefah? Ashe za ki neme mu?" Zuwa lokacin makota duk ana maƙale ana kallon me ke wakana Larai da Asabe da ma wasu yaransu dake gida duk sun fito sai dai ita bata kai hankalinta kansu ba yayinda duk suke kuka. Hannun kawu ta riƙe tana jin yadda zuciyarta ke kakkaryewa tace "Dole na nemeku kawu dole duk inda zan shiga ku ne nawa, ko me za ku yi min ku ne dole na duk duniya ba ni da waenda suka fi ku. Tsoro nake ji... Tsoro nake ji kar ku ƙi karɓa ta.." "Ko a ya kika zo Afeefah wallahi ba zan ki karbarki ba a yanzu, na tuba na yi nadama mai tarin yawa, na roki Allah a salloli dayawa akan ya waiwayo mana dake ya sa ki tuna da mu. Don Allah, Don darajar Allah ki dubi girman shi ki yafe min Afeefah ki yafe min don Allah" Kai take gyaɗa wa ta kai hannu ta share mishi fuska "Na yafe maka kawu wlh duk na yafe muku Allah ya yafe mana gabaɗaya" Inna Asabe ta rarrafo "Afeefah don Allah ki yafe mana don Allah" Ta kallesu sai ta ga inna Larai na ja da duwawu kafa ɗaya kam babu gabaɗaya kuma ba sanda bare wheelchair zubewa tayi tana neman yafiyarta duk ta yafe musu, Rayyan da ya gaji da kukan ya taho ya ɗaga ta tsaye yana kallon cikin idanunta ya fidda hanky fari tas mai cike da kamshi ya fara ɗauke mata hawayen fuskarshi babu ɗigon walwala. "Am sorry" Ta faɗa a hankali. Iso aka yi musu sai dai duk gidan an rasa ma taburma mai haske da za'a iya shimfida musu su zauna, Rayyan take kallo ta juya ta kalli kawu ta sake kallon Rayyan. "Ko za ka tafi mota ka zauna Ya Saraki?" Ya harareta ya samu wani dutse ya zauna a kai ta mayar da kanta ƙasa ko wannan kaɗai ya isa ta yafe musu, wa zai ce Rayyan zai iya zama a irin wurin nan saboda ita? Saboda kawai tana wurin idan ba don haka ba me haɗin kifi da kaska? Rayuwar mutanen gidan sossai ya chanza mata ko da ta ji irin neman ilimin da kawu ke yi tun daga sanadiyar yan shan jini da suka kama shi Allah ya nufe shi da shiriya ta tabbatar da gidan sun rabauta don ilimi shi ne ginshikin rayuwa, yaranshi duk sun dawo kan hanya sai talauci da yayi musu matuƙar yawa don Allah ya jarabcesu da babu tun bayan tuban shi abinda za'a ci ma wahala yake sai dai basu daina neman ilimi ba kuma dayake tuban gaskiya suka yi yana iya yinshi ya ga an ci wani abu ko da sau ɗaya ne a yini, tayi kuka har sai da Rayyan ya fara yi mata faɗa ganin da gaske ranshi ya ɓaci ya sa ta daina, ta basu labarin duk abinda ya faru da ita har kawo yau "Allahu Akbar... Allahu Akbar kabiran lallai shi mahakurci mawadaci ne kuma mai haƙuri shi yake dafa dutse... Yanzu Afeefah har 'ya'yan sarki mai tarin daraja biyu ne a gidana ta sanadiyar ki? Ashe ke ce kike gina wannan tamfatsatsen gini da masallacin juma'ar da babu irinshi a wannan gari? Allah mai girma Allah mai yadda ya so" Kawu ke magana cikin hawaye da tabbatar da girman zatin ubangiji. Kallon Inna Larai tayi tace "Kawu me ya sameta?" "Maciji ne ya sare ta mun yi gargajiya har mun gaji kafan ya rube dole muka nemi taimako dai da kyar muka hada kudi aka yanke kafar sai dai babu kudin ko sanda ne bare kujeran guragu a dole take yawo a haka da ja da duwawu" Lokaci Ryan ya kalla ya mata umurnin su tafi ana jiran su wurin taron da suka gayyata, kawu da iyalan shi duk suka tafi dasu wurin taron kusan duka jama'ar garin suna ɗakin taron barin ma fankoki dake kaɗa su ya sa sai nishadi suke. Mai gari ne ya fara yin bayani da kuma godiya ga wacce ta dubi garin ta zaɓi inganta rayuwarsu ta hanyar ba su ilimi wanda ta wannan hanyar ta riga ta gama musu komai, da ya zo wurin kiran suna sai ya ce "Wannan ɗin ba kowa ba ce illa mata ga Ciroma Sameer, Ciroma mai jiran gado kuma Yariman Matasa na ƙasar Fombina Afeefa..h Afeefah kamal??" Sai yayi saurin kallon matar da ake cewa ita ce Afeefahn, duk yan garin ido suka zuba mata suna mamaki da ikon Allah, wasu kunya na rufe su a yayinda tayi murmushi ta miƙe ta haura podium ɗin ta karɓi mic "Dukkan yabo da godiya da kirari sun tabbata ga Allah, taimakonsa da gafararsa muke nema, kuma muna neman tsarinsa daga sharrin kawukanmu da munanan ayyukanmu. Wanda Allah ya shiryar babu mai ɓatar da shi, wanda kuma ya ɓatar to babu mai shiryar da shi. Kuma ina shaidawa babu abin bauta da gaskiya sai Allah, shi kaɗai ne ba shi da abokin tarayya. Kuma ina shaidawa cewa, Annabi Muhammad bawansa ne manzonsa ne. Bayan nan ina yi mana Sallama irin ta addinin musulunci shi ne Assalamu Alaikum warahmatullah" Duk suka amsa, ta ɗan sauke numfashi "Ba gixo ba kuma ba mafarki ba haƙiƙa ni din ce Afeefah kamal wacce kuka fi sani da Annoba ko kuma Mayya a wannan gari, haƙiƙa na jure abubuwa dayawa daga gare ku 'yan uwana, yayyena, Ƙannene na da kuma iyayena. A baya na zama mujiya cikin tsuntsaye Abar kyamata da gudu. Abar tozarta wa da wulaƙanta wa, Abar muzantawa a cikin al'umma saɓanin a yanzu da nake da miji nagartacce nake kuma da surakan girma waenda suka taka rawar gani bisa inganta rayuwata daga Wacce ta sallamar da farin ciki ta sallamar da jin daaɗi zuwa wacce ta zama mai cike da buri da alfahari. Da na zauna nayi nazari da tunanin Meyasa nawa iyalan kuma dangina suka yi min abinda suka yi a baya sai na fahimci babu wani abunda ke damun ahalin wannan gari na mu sai rashin ilimi da sanin daidai. Na fahimci mun samu tawaya da koma baya a wannan ɓangaren iyayen babu bare su tarbiyatar da yara akan daidai, a sadda na sake zurfafa tunanin me zan yi na taimaki al'ummata sai na ga babu abinda ya fi dacewa irin in wayar mana da kai in taka rawa wurin ganin mun samu ilimi har ma muna aiki dashi, in ga cewa wata mace ko wani yaro bai ɗanɗani irin ɗacin da na ɗanɗana ba, in ga cewa yadda rayuwata ta inganta kowa ma a yankina rayuwarshi ta inganta gobenmu mu samu tsatson da za mu yi alfahari da su daga wannan gari namu. Ya ku 'yan uwana musulmai ku sani cewa addinin musulunci addini ne na ilimi. Umarni da neman ilimi shi ne farkon abin da Allah Maɗaukakin Sarki ya umarci Annabinsa (S.A.W) da shi, yayin da ya saukar masa da faɗinsa : ‫)اْقَر ْا ِباْس ٍم َر ِّبَك اَّلِذي َخ َلَق! َخ َلَق اِإْلْنَس اَن ِمْن‬ ‫َأْل‬ ‫ َعَلَم‬4 ‫ اَّلِذي َعَّلَم ِباْلَقَلِم‬3 ‫ اْقَر ْا َوَر ُّبَك ا ْكَر ُم‬2 ‫َعَلٍق‬ .[١ - ٥ :‫( ]العلق‬5 ‫اِإْلْنَس اَن َما َلْم َيْعَلْم‬ Ma'ana : (Ka yi karatu da sunan Ubangijinka da ya yi halitta. Wanda ya halicci mutum daga gudan jini. Ka yi karatu kuma Ubangijinka shi ne mafi karamci. Wanda ya sanar da alqalami. Ya sanar da mutum abin da bai sani ba). (Alaq : 1 - 5) Addinin musulunci ya kwaɗaitar da mabiyansa akan neman ilimi, domin ba zai yiwu mutum ya bauta wa Allah ba sai da ilimi. Allah madaukakin Sarki yana cewa : )28‫] (ِإَّنَما َيْخ َش ى الَّل ِمْن ِع َباِدِه اْلُعَلَماُء‬:‫فاطر‬ TA]. Ma'ana : (Kaɗai waɗanda suke jin tsoron Allah daga cikin bayinsa su ne masu ilimi) Idan na ce zan kawo muku faɗar Allah da kuma hadisan da suka yi magana akan ilimi da amfaninsa gare mu za mu kwana bamu ƙare ba amma tabbas da akwai ilimi da duk ban fuskanci abinda ya faru da ni a wannan kauyen namu ba, Ajalin mahaifina ya same shi ba tare da na zo duniya ba, mahaifiyata ta rasu bisa rashin kula da rashin zuwa asibiti a yayin daukar ciki zuwa haihuwan gida, kakata shekarun ta ya ja ƙwarai wacce dole a yi mata tsammanin mutuwa a sadda ta tafi haka Goggona ta tafi bisa sakaci da zaman jahilci da dabbanci da ake yi a cikin gidanta, bamu san kan mu ba bare mu nemi sanin hakkoƙin da suka rataya mana, hakkoƙin matayenmu, hakkoƙin iyayenmu bare hakkoƙin 'ya'yayenmu wanda duka sai ta hanyar ilimi za mu sani, na koma wurin Aunty zainabu ta gamu da postpertum wanda ciwo ne da ake samun shi bayan haihuwa duba da bata taɓa ba ga yawan shekaru babu wanda ya fahimci hakan sai da lokaci ya ƙure ta tafi duk ba mu dubi ajalin su ne yayi ba, mun manta Allah ya ce ba zai taɓa jinkirta ajalin dayanmu ba idan ya zo dole za mu tafi. ku sani na yafewa kowannenku da wanda yayi min na sani da wanda ban sani ba duk na yafe muku, a wannan gidauniya tawa tafiyar duk na neman ilimi ne da kuma tsayuwa akan kafafunmu don Allah ina roƙon mazaje da ku bar matayenku da ma ku karan kanku ku nemi ilimi don Allah ba ya ƙarbar uzurin bawa akan rashin sani saboda ya mana umurnin nema. Akwai ma'aikata da za su koyar da sana'o'i ga yara da matayenku su ma ku bar su don zai amfani wannan al'umma tamu, duk lokacin yaye ɗalibai idan yayi zan zo kuma idan Allah ya amince za mu dinga raba kyaututtuka da suka shafi sana'ar da mutum ya koya don ya cigaba daga inda ya tsaya ina Fatan ganin chanji daga gare mu bakidaya na gode" Wasu hawaye suke yi suna tuna abinda suka mata amma dayake tana da zuciya mai kyau dubi Alkhairin da ta nufe su dashi, kawu ta miƙawa mic ɗin don ya taso yana son yin magana, a gaban tarin al'ummar yana kuka ya ba da duk labarin abinda yayi mata da wanda aka mishi ta sanadiyar son zuciyarshi da yadda ilimi ya sauya shi daga mummuna zuwa kyakyawa har ya kara da "An karɓo daga Kasir ɗan Qaisi ya ce, ina zaune tare da Abud Darda'i a masallacin Dimashqa, sai wani mutum ya zo wajensa ya ce masa, Ya Abud Darda' i na zo wajenka ne daga Madinar Manzon Allah (S.A. W) saboda wani hadisi da aka ce min kana faɗa daga Manzon Allah (S.A. W), kuma babu wata buqata da ta kawo ni nan sai wannan. (wato jin wannan hadisin) Sai Abud Dar' da'i ya ce, "Na ji Manzon Allah (S.A. W) yana cewa : "Duk wanda ya bi wata hanya yana neman ilimi a cikinta, to Allah zai sanya shi akan hanya daga cikin hanyoyin Aljannah, kuma haqiqa Mala'iku suna sanya fika - fikansu ga ɗaliban ilimi, don yarda da abin da yake nema, sannan duk wanda yake sama da qasa yana nema wa malami gafara, har ma da kifayen da suke cikin ruwa. Falalar malami a kan mai bauta kamar falalar wata ne a daren goma sha hudu a kan sauran taurari, kuma haqiqa malamai magada Annabawa ne, Annabawa kuwa ba su bar gadon dinari ko dirhami ba, kaɗai sun bar gadon ilimi ne don haka don Allah kar mu raja'a akan boko don shi iya na duniya ne mu nemi lahira kuma mu koyar komin kankartarsa, ko uwa malama ce akan yayanta kar mu saka finafinai ko waƙa gaba mu ta rawa da nishadi da yara mu koya musu abinda zai amfanesu a gaba. Ni a karan kaina misali ne kuma Aya ne ubangiji ya nuna min akan Afeefah" Duk jikin mutanen wurin yayi sanyi kuma sun gamsu ɗari bisa ɗari da lallai suna da nakasu ta wannan fannin dole rayuwarsu ya tafi a jiɓance, Afeefah da manyan gari a gefenta mijinta ne da ya bata support ɗari bisa dari suka zaga wurin tassss ta yabi kyau da tsarin komai na wurin kuma duk abin bukata akwai. Kawu ta damƙawa wurin ta ce ta bashi amana ya riƙe mata ya kula da komai yadda ya kamata bisa tsari shi dai babu bakin magana don ya rasa me zai ce. Cikin jami'an tsaro masu kula da taron kawai idanunta ya sauƙa kanshi, da sauri ta nufe shi tana kallonshi shima ita yake kallo a hankali ta nuna shi "Sa'adu? Sa'adu Rabi'u kai ne?" Kai ya gyaɗa yana murmushi ya gane ta amma bai zaci zata nuna ta sanshi ba ta juya ta kalli Rayyan ya matso "Ka tuna shi Ya Saraki?" "Wannan police da ya ceceki daga sharrin gurbatattun 'yan uwansa" Za Ta cire zobenta na gwal ya miƙa hannu ya riƙe nata, ya zari kati daga aljihunshi ya miƙa mishi "Ka ƙira ni in shaa Allah kyautarka ya fi karfin kuɗi za'a mayar da kai cikin Kaduna da matsayi mai kyau" Hawayen murna ya fara yana godiya. Ko da aka watse taron suka koma gidan Kawu akan za'a saka date na fara daukar ɗaliban da suka kamata za kuma ta turo waenda za su taimaka mishi wurin fahimtar komai da komai kan a sakar mishi, a tsakar gidan suka samu an jibge kayan abinci babu abinda babu wanda za su iya ma watanni goma zuwa ashirin basu nemi kayan abinci ba, a gefe crouches ne da wheelchair na inna Larai Afeefah tayi saurin kallon Rayyan ya girgiza mata kai yana dan ɗage kafada sai ya juya ya fice ta bi bayanshi Za tayi magana jiri ya ɗan dibeta da sauri ya riƙo ta "Boɗɗi menene? Ba kin ga illar kukan da kika dinga yi ba duk yau kin tarawa kanki damuwa! Kan na ciwo ne?" Ya kai tafin hannunshi yana dafe goshinta hawayen ta sake farawa "Ban san da wani baki zan fara maka godiya ba Ya Saraki... Ko baka faɗa ba na san aikinka ne Allah ya biya ka ya saka maka da alkhairi ka yi min komai Ya Sa..." Hannunshi ya sa ya rufe mata baki yana dan ɗauke hawayen da take zubarwa yace "Kin chanchanci fiye da haka a gareni Afeefah don haka ba komai ba ne, na so ko gidan haya ne mu kama a gyara wannan amma bai samu ba idan ba damuwa za su dan koma Kaduna ko ma su je ganin ɗakin ki a Fombina kan su dawo sai a gyare nan ɗin" Rungume shi kawai tayi ya sa hannu yana dan shafa bayanta kan ta ɗago sai ta sake jin jirin yamutsa fuska tayi, ya shiga mota don bai kula ba itama ta zaci ma stress ne don haka ta koma ta musu bayanin za su je Fombina ko sati biyu su yi za'a ɗan gyare nan ɗin kuka kam kawu har ya rasa hawaye ya rasa bakin godiya a haka suka ɗauki duk abinda za su ɗauka aka adana kayan abincinsu a daki guda suka ɗauki duk wani abu mai muhimmanci, yaranshi maza manyan uku da mata shidda na Inna Asabe uku na Inna Larai biyar suka bar garin zuwa Kaduna. Kai tsaye gidan Mammi suka yi masauki jannah ta turo abinci ko da Abeeha ta gaya mata da baƙi suke ta turo daga restuarant, a masaukin baki aka sauke su suna ta mamaki da santin gidan, Ita dai Afeefah su Suhaila ta ja zuwa ɗakinta ta musu wanka ta duba cikin tsarabarsu da ta musu na musamman ta fidda kaya ta saka musu suka haɗe babban parlor aka ci aka sha kan kowa ya nemi makwanci don sun gaji, sai da ta tabbatar sun yi bacci ta watsa ruwa ta shirya cikin wani Red kayan bacci da yayi mata kyau sossai marabarshi da babu kaɗan ne ta nufi ɗakinshi... Yana jingine da gado yana jiranta suna haɗa ido suka Sakarwa juna murmushi mai ƙayatarwa, yanga tayi ta mishi Dukda kunya dake ɗawainiya da ita barin killer looks da yake binta da su har ta iso gadon ya fusgo hannunta ya manna ta kirjinshi yana matse ta a lokaci ɗaya suna sauƙe ajiyar zuciya a tare A kunnenta ya raɗa mata "Kina kashe ni da raina Gimbiyata" Ta ɗan ɗago bai tsammata ba ta haɗe lips ɗinsu kaman jira kuwa ya mirginata kasanshi ya mata rumfa yana bata wasu kisses da suka sake matar da ita a kaunarshi hannunta na yawo bisa bayanshi zuwa keyarshi tana mishi susa, gasping air yayi ya raba lips ɗin suka yi murmushi mai sauti ya sake mayar da lips ɗin yayi mata kyakyawar Kiss Ta raba fuskansu tana shafa kanshi hancinsu haɗe da juna suna musayar numfashi ta ce "Na gode sossai Na gode kwarai haƙiƙa Allah ya wanke min zuciya ya ba ni mijin marainiya, ya ba ni kai ba tare da wayo ko dabara ta ba a koyaushe ba ni da abin faɗa a gareshi sai Alhamdulillah. Ina roƙon Allah akan duk ranar da za ka haɗu da shi, Fuskarka ya zama mai annuri da sheki fiye da yadda yake a yanzu, ya rabautaka da karɓar kyawawan sakamakonka a cikin tafin hannunka na dama sannan ya ce "I am pleased with you" ya haɗa mu gabaɗaya a aljannah madaukakiya ya ba ni dama da ikon Zama shubagar matayenka a aljannah. Ina ƙaunarka Ya Sameer...Ina ƙaunarka Ya Rayyan ina matukar sonka Ya Saraki" Hawayen dake zuba mata yake bi a hankali da harshen shi yana ɗaukewa cikin wani salo zuciyarshi ƙal yayi fixing gaze ɗin shi cikin idanunta "I love you. love you more than anything Afeefah, ban taɓa jin son wani abu yadda nake jin naki ba, I love you more than myself. I will always love you. I will love you till the end of my time. No words can express how much love i have for you. I will alwavs be here for you no matter what kin ji? Babu abinda zan miki da zan ji yayi yawa you are my favorite girl nd my only blessing" Daga nan ta dafa chest dinshi sai ya koma kwance ta dane jikinshi da kanta ta shiga gigitashi abinda bata taɓa sakewa tayi ba ta yi shi a ranar ta goge mishi hadda sai gashi yau ma yana yi mata kuka don ta gama da rayuwarshi in dai ta fannin ne. Washegari sun tashi da mummunan labari don Uncle Usman ya rasu labarin ya kaɗa ta don faɗuwarta kawai suka ji hankalinsu ba karamin tashi yayi ba barin ma Rayyan a hannunshi ya ɗauketa suka tafi asibiti don duk abinda za su yi sun yi matsayin shi na likita ya kasa farkar da ita yana jin panic akan ciwon Mammi amma bai san Meyasa duk abinda ya shafi Afeefah na fitar da ragwantakanshi a fili ba, tsoro da fargaba ya sa ya manta yadda ma ake aikin likitacin sai a asibitin ne aka samu ta farfado nan suke samun labarin tana da shigar ciki kuma razanar da tayi har ya fara barazana ga ɗan cikin nan ya saka aka yi mata allurar bacci don ta huta sossai. 'Yan uwanshi sun yi rawan gani da su Sulaiman aka sallaci uncle Usman aka kai shi makwancinshi dogon takarda da ya roki sulaiman rubuta mishi ya ba Rayyan akan idan ta dawo daidai sai a bata. Kwanan ta biyu kan ta dawo cikin hayyacinta tayiwa su Suhail kuka ba na wasa ba don maraici babu daaɗi ta kuma yi alkawarin rike su fiye da ƴaƴan cikinta har illa masha Allah. A kwana na huɗun suka juya Fombina, anan ne Kawu suka san basu ga komai ba baki sake suke bin irin girma, tsaruwa da ma kyaun masarautar irin mulkin da ake shimfidawa ko a mafarki basu taɓa mafarkin halartar irin wannan wuri ba sai gashi wacce suka raina ta zama sanadiyar da ake zube musu, sun yi kuka kaman me don sashe na musamman aka sauke su mai martaba da Ammi suka tura ake musu hidima wane wasu masu kuɗi. Ammi da mai martaba kaman su hadiye Afeefah jin labarin cikinta, soyayyar mijinta kuwa ya ninku fiye da yadda yake jinta a da su Suhail sun zama 'yan gata don a take aka tsara musu dakunansu Mai martaba ya sa aka cike musu wardrobes da kaya Ammi ma ba'a barta a baya ba don abinda za ta yiwa jikokinta shi take musu har ma sun Fara ƙiran Afeefah da Ammah Ryan kuma Abbu, school na musamman ya saka su masu musu hidima ma daban aka ware don Afeefah laulayi mai wahalarwa take. Satin su Kawu uku suka koma bayan Rayyan ya saya mishi babban waya an hada su da goma sha tara na arziki suka koma, gidan su ya zama daga cikin gidajen da suka fi kowanne kyau a garin ɗan daidai kuma a kayace sai ya tuna akurkin da suka warewa Afeefah take rayuwa lallai Allah ya nuna musu ikonshi sun tuba har sun rasa bakin tuba, a kuma satin da suka koma aka fara gudanar da aikin gidauniyarta. Sai ga kujerar Umura da Rayyan ya biya musu har da su Mai martaba za su tafi da su Abeeha, sun yi murna barin Afeefah da bata taɓa zuwa ba za dai tayi kewan yaranta cikinta na wata huɗu suna gama second semester exams suka chale ƙasa mai tsarki ranar da ta fara ganin ka'aba tayi kukan da sai da tayi zazzabi bata taɓa ganin abu me kyau da natsuwa ba irin shi duk rayuwarta, ta zube wurin ta yiwa iyayenta da yan uwanta da ta rasa Adu'a har sai da miyaun Bakinta ya kafe, sun yi sati uku chan sayayyan baby kuwa kowa yi yake ba Ryan ba ba Ammi ba ba su jannah ba, daga Saudi sun tsaya kaɗan a Turkey sun yi sayan kayan ɗakin su Aisha ana dawowa Nigeria Aka fara hidimar bikin su. 🖤Gureenjoh🖤 HAIHUWA DA HANJI (A True life story) Fatima Muhammad Gurin (Gureenjoh) Wattpad-Gureenjo6763 Arewabooks-Gureenjoh ADABI WRITERS ASSOCIATION *FREE BOOK* *Wannan shafin naki ne Uwar Ɗakin Damisa namu angon Nyla Ƙani ga Didi kuma Uban Didi. Nana Halima ko na ce Leemar's delicious mai abincin 'yan gayu...Allah ubangiji ya ƙara miki basira da hazaƙa ina godiya ƙwarai🥰* *FINAL PAGE* *60* Zaune suke a cikin ƙayataccen hall ɗin da ake shan hidimar bikin Autan Mammi da Autar Ammi waenda duk yanzu suka zama shalelen Ammi kuma angwayen ma duka 'ya'yanta, Ryan na zaune bisa wani table riƙe da hannun Afeefah sun yi azabbaben kyau cikin outfit ɗinsu na Soire party wanda english party ne duk mazan shigar suite suka yi matan english dress, Farin suite ne jikinshi da baƙin shirt daga ciki bakin takalmi da baƙin hankey da ya ɗan leƙa bakinshi daga aljihun, gashin shi ya sha gyara ainun fuskarshi sheki yake kowa ya ganshi ya ga cikakken namijin da yake cikin kwanciyar hankali da jin dadi. Tana sanye da wani doguwar riga na tsadadden sugar lace da ya bayyana cikinta da ya taso yayi mata kyau ainun, ta saka gyale da ya tafi da kayan tayi wrapping kanta ta sha make up da ya matuƙar zama mata wanda mijin nata ke ta bacin rai akanshi don kishi ya sa ko motsi tunda suka zauna basu yi ba su Saleem sun ta kiranshi ya ƙi zuwa sai Sulaiman ne yake representing ɗin shi, gabansu Suhail da Suhaila ne shigan ryan shine irin na Suhail haka Suhaila ma irin na Afeefah sai suka ba da wani kyau mai ma'ana. Zarah ce da yanzu ta sake saboda janta da su Abeeha ke yi a jiki kuma tayi tuban gaskiya ta zo ta ja su Suhaila don tana kaunarsu su ma kuma sun sonta, Afeefah ta kalli Ryan "Ya Saraki..!" A Shagwaɓe tayi maganan ya kalleta "Matar Masu Sarauta ya aka yi?" Yayi maganan yana ɗage mata gira tace "Eyyaa dubi ana yi wa Adda Abeeha barin kudi in je in manna kaɗan mu yi hoto?" "Wanda kuka yi kan ku zo nan ya isa ba za ki shiga cikin maza ba" Ta ɗan ɓata rai har ma nadamar Kwalliyar take ji yadda ya kasa ya tsare dama bikin duk ya hanata wani hidima yadda ta so cin uwar sabada sai dai ta ga su Samha na yi don duk Fombina suka zo har Sadiqa da ake hidimar aurensu tare sun zabi su zo nan in za'a ɗaura aurenta sai ta koma tunda sai an ɗaura na Saleem an kai mishi matarshi zai ba da nata. Har su kawu sun zo bikin da Inna Asabe sun bar inna Larai a gida, kawu ya sauya ƙwarai natsuwa ta shige shi haka Inna Asabe da inna Larai babu wannan rawan kan da son zuciyar sam sam sam. A bikin ne ma take samun labarin Sabrina da iyayenta inda ta kwaso HIV da ya kasa warkewa ga talauci da yayi musu katutu ita Gaje garin zuwa boka nema mata waraka ta faɗo daga tsauni sai gawa aka ɗauka Yaya ne ya zo neman tuba wurin mommy kuma ta yafe musu. "Assalamu Alaikum warahmatullah" Wata ƙawar Aisha ce ta yi musu sallama, Afeefah ta kalleta da mamaki don ta kula yarinyar na ji da uban ta wani ne tun fara bikin sai rawar kai take bata zaci Rayyan zai wani kula ta ba sai ta ji ya amsa, a take wani abu ya taso mata zuwa wuya wato ita ce bata da kishi shi ya hanata tashi saboda maza ita kuma tana kallonshi yana magana da wata macen. "Yayanmu barka dai, mun jima muna kallon irin kokarin ka akan rayuwar matasanmu a koyaushe His Excerllency ba shi da zance sai taka gaskiya samun shugaba irinka abin alfahari ne in kuwa da irin ku rayuwar matasanmu ba zai taɓarɓare ba" Ya san mahaifinta Gomna ne mai ci a yanzu don haka yana martaba gidansu sai ya ɗan murmusa "Thank you" "idan ba damuwa ga wannan na jima ina so na baka ban samu ganinka ba Its a small gift don Allah kar ka ce a'a" Ta ajiye wani karamin paper bag tayi murmushi ta juya ta wuce. Kaman an ce ya kalli Afeefah ta haɗa gabas da yamma kudu da arewa, idanunta har shekin kwalla su ke, hannunshi dake cikin nata ya ɗan murza don ta kalleshi amma ta ɗauke kai sai ma ta miƙe chadak ta nufi waje, da sauri ya bi bayanta yana dan kiranta amma bata waiga ba dab wurin mota ya riƙo damtsen hannunta a hankali ya janyota bayanta ya sauƙa kan kirjinshi yana dan lekan fuskanta yace "Tsaya mana Boɗɗi fushi kika yi?" Fuskarta babu walwala ta janye tare da Juyowa ta kalleshi "No, Meyasa zan yi fushi?" "Me yasa kika fito to ina ta magana kin ki kulani?" Ta kalleshi "Gashi na kula ka, ina jinka" Numfashi ya sauke "It seems kin gaji mu tafi gida" Ta juya ta nufi motarshi bata ce komai ba, numfashi ya sauke yana ɗan shafa gira ya nufi motar tuni ta buɗe ta zauna ya shiga shima drivern shi ya ja suka nufi ɓangaren su tunda akwai tafiya sossai, hannunta ya riƙe ta zame tare da juyawa tana kallon Window. "Akwai abinda ya faru ne? Ko na miki ba daidai bane?" "Babu, me kuwa zai faru?" "Ta ya zan sani Afeefah na ga kina fushi" Ta ɗan bashi side eye tana sake juyawa "Ni ba fushi nake ba" Lip dinshi na kasa ya ɗan lasa har ga Allah bai zaci wai kishi take ba a hankali yace "Ok" Ya kalleta sai ya ga ta sake haɗa rai ya sauke numfashi har suka isa ta sauƙa tun kan ya zagayo ya buɗe mata. Ɗakinshi kai tsaye suka nufa don suna shiga parlorn ya riƙo hannunta, bata ga amfanin make up ɗin ba bayan hotunan da suka yi musamman nata dashi da yayi kyau ainun hannunshi kan cikinta yana murmushi yalwatacce ita kuma tana kallon hannun nashi tana murmushi wanda har ta mayar wallpaper to bayan shi bata ga amfanin adon ba. Wanka ta shiga bayan ta goge Kwalliyar shima ya kwaɓe ya bi bayanta, tana tsaye shower ta ji ya manne da ita yana bin wuyanta da tafiyar tsutsa, zamewa take har ta gama ɗauraye jikinta ta fice ta bar shi ya bi bayanta da kallo, bata wani tsaya drying kanta ba ta duba shirt din shi ta saka don tana jin daaɗinsu sossai ta zame towel ɗin tana bottuning shirt ɗin da iyakarshi rabin cinyarta ya fito ɗaure da towel a kugunshi da wani irin kallo yake binta ganin ta nufi bakin gado ya isa ya kama hannunta "Kina so ki yi mura ko?" Bata tanka ba yaje ya ajiye ta gaban madubi ya zaro hand drayer ya shiga busar mata da gashin cikin kulawa. Miyau take hadiyewa tana bin ginannen jikinshi dake bayyane da kallo, ganin zai kalleta ta ɗauke kai yayi murmushi ajiye drayer ɗin yayi ya duƙa sossai yana shunshunar wuyanta da baya rabo da kamshin da yake masifar so, a yanzu har da lips ɗin shi yake goga mata zuwa sajenshi da ya sa duk numfashi na kwace musu barin ma shi da yake a kunne, hannunshi ya mayar ta gaban rigar nashi dake jikinta ya fara unbottuning saman shirt ɗin yana sauke wahalallen numfashi mai rikitarwa. "Ya Saraki ka bari, bacc..." Hannun da ya tura cikin rigar ya sa ta ɗauke numfashi ganin zaunen ba zai kai su ba ya ɗagata chadak zuwa gado yana ƙarasa unbottuning shirt ɗin, tun tana resisting har ta sallamar suka rikice a duniyar masoya sai da komai ya kamallah ta zame za ta sauƙa ya dawo da ita yana shafa lallausar Fatan bayanta "Kika cigaba da fushin nan zuciyata za ta iya shiga matsala Ya Alami" (Duniyata) Yana cigaba da shafata a natse ya cigaba "A faɗa laifina in yi gaggawar tuba kin san Sameer mai biyayya ne a fadarki" Ta ɗan yi murmushi ta isa? Sarkin gobe ya zama bawan ta? "Shine har da yiwa wata murmushi a gabana har da karɓar gift ɗinta" "O'ooo am very sorry ban san dalilin fushin ba kenan, kin fa san babu macen da take da daraja ko kima a idanuna bayan ke da Ammi, Afeefah ke ce mahadina daga ke kuma Ryan ya gama kallon 'yanmata" Wani sanyi ne ke kwarara mata yana mata son da bata san adadin shi ba, ɗagowa tayi ta mayar da kanta kan pillown da yake sai ya juyo suna kallon juna tace "Na sani ba zaka taɓa zama da mace daya ba amma na rasa Meyasa duk sadda wata macen ta kallar min kai sai in ji mutuwa ne kawai ya saura mini tsabar zafin zuciya" Yayi murmushi yana riƙo hannunta a tsakiyarsu "Wa yace miki hakan?" "An ce sarakai ba sa zama da mace ɗaya" "Za'a fara a kan Sameer Muhammad Modibbo don daga ke na rufe kofa a gidana" Soyayyarsu suka cigaba da sha yana bata duk kulawarshi ta so ta tafi Kd ya hana don haka ta mayar da hankali kan lectures ɗinta da kulawa da shi da kuma cikinta har Allah ya kawo ta watan haihuwa, wani ranar Alhamis da dare labour ya saka su nufar asibiti babu shiri a safiyar juma'a ta santalo katoton ɗan ta fari tas mai kama sak da mahaifinshi wanda a ranar BOƊEJO ta sha kuka ganguna da kalangu sun yini dokawa kowa ya gifta Masarautar Fombina sai ya san ana cikin alkhairi dumu-dumu. Yaro ya zo da tarin alkhairi don Mai martaba ji yake kaman ranar ne ya fara riƙe Sameer a hannunshi tuni lungu da saƙo sun samu labari hotunan kuwa har ya je Kaduna uwar jego ta sha ƙauna iri iri, ko da suka dawo masarauta sashenta take wata dattijuwa ta shiga hidimar kula da ita da bata cikakken kulawa na masu jegon gargajiya, ranar suna an yi bidiri Aisha ta zo da cikinta kuwa haka sulaimi ma ta zo da nata tamfatsatsen cikin Haihuwa yau ko gobe sai Jannah da take shirin zuwa amma labour ya hanata itama a ranar sunan ta haifi danta namiji, Abeeha ma na fama da laulayi aka yi hidimar suna na ji da gani kuwa yaro ya ci suna Muhammad Sameer Modibbo. A daren sunan Rayyan ya tafi Kaduna don da Jannah ya yini, Ammi ma da kanta ta tafi da wasu hadimai duk basu dawo ba sai da aka yi suna suka bar mata hadimar da zata kula da ita mai martaba ya aika sha tara na arziki inda yaro ya ci sunan Rayyan. Bayan sunan Muhammad da suke cewa Arham Sulaimi ta koma da sati biyu itama nakuda ya tashi mata sai dai she didnt survive bayan ta haihu Allah ya karbi ranta sun shiga tashin hankali dole Afeefah suka tafi Kadunan duk sun yi jimamin mutuwar ba kadan ba, inda Sameera ta samu Saleem ta roƙe shi ko don 'yar da ummu sulaimi ta bari tana so ta auri Sulaiman ta shayar da yarinyar kaman na ta. Kan Sulaiman ya amince Umman shi ta amince aka daura musu aure kuwa babu wanda ya hanata shan kwayoyin da ruwan nono ya zo ta shiga kula da ummu sulaimi ƙarama don soyayyar da take yiwa Sulaiman shi ya dawo kan yarinyar kuma tana haƙuri don auren mijin matacciya wanda yake son matarshi sai a hankali. Baaba jummai da Afeefah kaman jiƙa da kaka don kusan kullum suna tare a waya kuma Daga ita har Rayyan da su Ammi su kan yi mata sha tara na arziki don kaman uwa take har a gidansu Sulaiman ɗin ba 'yar aiki ba. Rayuwa ya cigaba da juyawa ba za'a ce ba'a saɓawa ba sai dai duk abu da fahimtar juna ba karamin lasting yake yi ba, sossai rayuwar Afeefah yake kan saiti har aka wayi gari ta gama karatu inda ranar da ta gama last paper ɗinta ta shigo masarautar ta sauƙa a sashensu kawai ta ga wata hadaddiyar tsadaddiyar Maybaach Ash Color an yi mata ado da furanni, Rayyan ta gani ya fito cikin kyakyawar shiga fuskarshi ɗauke da smile yace "Congratulations Allah ya albarkaci abinda kika karanta My baby mama" Tsallen murna tayi fuskarta dauke da fara'a ainun ta karbi keyn ta buɗe motar sai taga balloons na zubowa kaloli daban daban Juyowa tayi rungumeshi cike da farin ciki take cewa "Thank you so much My love, My best friend, My for ever, My safe space. Thank you for being you and choosing me everyday.." kan yayi wani motsi ko magana sai ta fara jin tashin trumpet ana yi mata congratulations tana juyawa ta ga abokan arziki na kusa da na nesa ta ma rasa yaushe suka zo kuma ta yaya? Ameer da Abeeha sanye cikin shiga iri daya Abeeha na rungume da ɗiyarta mai sunan Mammi ana kiranta Mamah bata wuce shekara da wata biyu ba, Jannah da Rayyan ɗinta da yake ma wurin shekara uku da wani cikin a jikinta, Saleem da Aisha da suke riƙe da wani Rayyan ɗin dan wata huɗu kacal, Sameera na tura ciki ga Ummu sulaimi da tayi wayo sossai gefen ta Sulaiman, ga Samha Amarya wacce bikin ta ne next suke ta planning don abin bai zo da wuri ba, sossai take murmushi tana kallonsu yayyenta ne, Ƙawayenta ne kuma 'yan uwanta ne... Hawaye taji ma tana ji a daidai sadda su Suhail su uku cikin shiga iri daya na kananun kaya suka zo suka rungume ta. "Congratulations Ammah" Ta ɗaga Arham ta na dariya sossai take cewa "Thank you love, na gode sossai" Rayyan ya matso yana dauke mata hawayen farin cikin da take, nan suka isa parlor abincicikka da cakes iri daban daban an ci an sha an yi hira kaman ba gobe, Rayyan dai baya cewa komai sai murmushi dama sun riga sun san hali Afeefah ce mai shan maganarshi idan ta ciyo shi. Sai dare suka watse ta fito cikin shirin kananun ƙaya wani half gown purple da ya amshe ta ya fitar da duk wani sura na jikinta, parlorn su kaman ba shine dazu kaca kaca ba hadimai sun gyare tsaff an cika turarukan wuta, ɗakinshi ta nufa bayan ta duba yaran sun yi bacci yana yana operating Phone ɗin shi hankalinshi ya ɗan dauku a chan jikinshi ba riga, tana isa ta sa hannu ta zame wayan ya ɗago ta jefa wayan kan gado tana murmushi sai ya saki baki yana kallon rigar na jikinta da ya fito da full chest ɗinta daga sama, rabin cinyanta duk a waje gashinta a ɗaure wuri guda sai sheki yake tana ta zuba kamshi bakinta da ta sa wani lilac lip gloss sai sheki yake, hannu ya wara mata ta kuwa tafi a slow suka yi baya baya tana kwanciya nashe nashe akan jikinshi don babu inda ya taɓa katifa a nata jikin, da hannunta take wasa da kirjinshi idanunshi a lumshe ya ce "Boɗɗi" "uhmm Boɗɗin Boɗɗi" Idanunshi da suke ta lumshe wa a mayen ƙaunarta ya buɗe don sunan ya mishi daaɗi 'kyakyawan mai kyau' "I love the name" "kai wani suna ne baka so?" Yayi murmushi mai sauti "Ai duk sunayen ne daga kin faɗa sai sun motsa zuciyar maza" Tayi murmushi tana tuna lokacin da yake mata masifa in ta kirashi Saraki ta ce "Shiyasa baka son na ce Ya Saraki?" Ya ja iska kadan yana furta "Aouchhh sunan ya fi taɓa ni but sincerely wani irin fusgata yake zuwa gareki in kika faɗa cikin wannan voice din naki mai daaɗi" Tayi murmushi yana zame ribbon ɗinta ya cusa hannunshi cikin gashinta ya ce "Faɗamin abu mai daaɗi" "I love you" Ya tsinci kanshi da lumshe ido yana jin kalmar straight to his heart. "Faɗi wani" "Ina sonka!" Tayi maganan tana wasa da sajenshi cikin susa mai daaɗi. "Sake faɗamin" "wani waƙa Naji da ya dace da kai in rera maka?" Gira ya ɗaga ta gyara kwanciyar ta akan jikinshi ta shiga mishi wakan "ka sace zuciyata! Kana kai mini gatah! Mata nai musu rata.. Ka ce in je in hutaaa.. Ga mijina mai tsafta Mai halin girma na sarauta Zama da kai sam babu wahalta..! Cikin mazaje ka cire tutaaa Mai adalci da nagarta..! Fushinka shi ke sa ni ɗimautaaa Mai haƙuri shi ke dafa dutsseee!!" Numfashi ya sauke muryarta wane sarewa haka ya buɗe idanunshi da suka mace a so yana kallonta a hankali yace "hakane kam mai haƙuri shi ke dafa dutse, nima na cire tuta tunda na same ki" Tayi dariya mai yanayi da giggle ya juya ta yana shunshunar wuyanta ta zura hannunta gashin shi tana ɗan kame jikinta tace "Toh ai ban gama waƙar ba fa Boɗɗin Boɗɗi" Ɗagowa yayi yayi pecking lips ɗinta chan ƙasa yace "Toh ƙarasa Babylove" "Kaine tsanina...maqabulina!! Kai ne rabin raina... Makasudina!! Kaine muradina.. Kai ne Farin cikin raina... Kai ne Al'amari babba... Kai ne Abin da duk zan ma.. So ne Murmushi in kai kyau neeee" Ya kuwa doka murmushin yana rasa wani baiti ne ma ya fi daaɗi, bakinsu ya haɗe ya shiga aika mata zazzafar Kiss cikin kiss ɗin ya ɗan zame yace "Nima ke ce farin cikin raina, ke ce muradina kuma ke ce rabin raina My Hayateee... Help me mu samu Mammin mu a daren nan" Kaman jira kuwa ta sakalo wuyanshi tana mayar da Bakinta cikin nashi. *BAYAN TSAWON LOKACI* Afeefah ce ke saukowa jirgi hannayenta rike da wasu 'yan mata kyawawa biyu, bayanta Suhail ne da Suhaila da za su yi shekara shidda zuwa bakwai sai Arham da yake huɗu da 'yan kai bayansu wasu hadimai ne guda biyu da suke taimakonta da yaran har zuwa wani prado baƙi wuluk a jere motocin huɗu suka fice daga airport ɗin sai fadar Fombina wanda a yanzu Laamiɗo Sameer Muhammad Modibbo ne ke kan mulki, Ƙashin bayan matasan Fombina, jagoran al'umma kuma jarumin Afeefah uba ga Ciroma Arham da 'yan uwanshi Garkuwa Fulanin duk Nijeriya. Isarsu tamfatsatsen sashen na Fulani Afeefah ana ta baza gaisuwa da ban girma tana amsawa cikin kulawa da kaunar al'ummar nasu kaman yadda suke masifar ƙaunarta, Ɗaya daga kyawawan yaran nan mace tace "Ammah mun dawo mu je wurin Abbu? I Miss himmmm?" Girgiza kai Afeefah tayi "Abbu na cikin taro Alhan, ki bari anjima idan ya dawo sai ki ganshi ko Mammin Abbu?" Ta ɗan tura lips Ɗayar tace "Ammah to mu je wurin Jadda?" "Ku fara yin wanka Ahlam sai ku je na san ta yi missing surutunku" Da gudu suka yi ɗakinsu daman yan mazan sun jima da wuce wa yanzu haka bai wuce sauri suke suyi wanka su tafi wurin Abeey ba dake ji da su. Ɗakinsu ta wuce ita da mijinta don bai wani yarda da raba sashe ba tunda har yau bai yarda ya karbi auren wata ba duk kuwa da tallar da ake mishi tun kan Abeey yayi murabus ya bashi har yau, ya ce duk abinda zai nema ya samu a wurinta to na me zai sake aure? Me kuma zata bashi banda ta nemi daga mai hankali? Afeefah na iya kokarinta wurin ganin ta bashi Kulawa, soyayya da lokacinta bata aikin komai banda gidauniyarta kuma duk ba ita ke kula da komai ba sai in ya kama don haka tana da lokacinshi full kuma bai taba neman ta ta ƙi ba a koyaushe burin ta ta faranta mishi ko da har ranta bata so. Tana zame kayanta ta ɗaura towel zata shiga wanka kawai taji an yi hugging ɗinta kamshinshi da numfashin shi ya sanar mata waye, fuskarta washe da murmushi tace "Sarakina" "Matar sarki, barka da dawowa ga masoyinki" Ta waigo tana Shagwaɓe mishi "Ba wani bayan ka gudu ka baro mu Abuja" "Kin san ba da son raina bane hakan da a sona na ne da kowa ya tafi ya bar mu mu biyu a duniyar nan" Dariya tayi Yace "Ya taron na ganku a Tv i hope komai ya tafi lafiya?" "Alhamdulillah wannan kam ya ƙare saura na Lagos" Girgiza kai yayi "Babu inda za ki je, ki wakilta wata ko wani su je miki" Karkata wuya tayi "Har kaduna? Ka ga fa akwai sunan Ɗan Samha ga yaye ɗalibai da za'a yi a gidauniyarmu na Dutsen-wai karo na wurin bakwai akwai kuma taron buɗe wani a Anchau" Girgiza kai yayi "Ba zan juri nisa dake ba, wai har ma gidauniyar nan nawa za ki buɗe ne?" Tayi dariya yana daukar ta chak suka nufi toilet don yayi mata wanka yana tambayarta Ammi da Mamminshi fa tace sun tafi sashen Jaddansu(Ammin) Suka shige cikin bahon wanka suna cika juna da kauna, tana daga cikin matan manya da ake ji dasu saboda taimako, iya ado da shigar kamalarta, haƙuri da iya maganar ta don duk tayi magana a taro sai ya kwana biyu yana circulating platforms, karama ce mai halin girma kaman yadda mijinta yake ƙarami cikin sarakunan yankunan Arewa sai dai akwai zuciya da kwarjini, idan suna tafiya a tare za ka zaci ɗawisu ne yana baza ado gaban 'yar budurwar ɗawisunshi, komai ya wuce a rayuwar Afeefah da har in ta tuna baya sai dai tayi murmushi su kawu na chan Dutsen-wai har yau sai dai ta kai musu ziyara ta dawo. Dafa ita har Rayyan sun yi sadakatul jariya da sunan iyayenta da Mammi har basu san adadi ba. Ta samu akallah gidauniya 10 da ake bata taimako daga masarautu zuwa gomnatin jaha har na tarayya sun san da zamanta, kasancewar gidauniyarta dake tallafawa mata da yara akan neman ilimi, sana'o'i da tsayuwa akan kafafunsu kuma dama babban burin ta kenan mutane su samu ilimi kuma suna samu daidai gwargwado Alhamdulillah. ALHAMDULILLAH! ALHAMDULILLAH!! ALHAMDULILLAH!!! ANAN NA KAWO KARSHEN WANNAN LITTAFI NA HAIHUWA DA HANJI ABINDA MUKA RUBUTA DAIDAI ALLAH UBANGIJI YA BA MU LADA WANDA MUKA KUSKURE ALLAH UBANGIJI YA YAFE MANA. HAKIKA TAFIYAR NAN NA DAGA CIKIN TAFIYAR DA YA MATUƘAR YI MIN DAAƊI BISA GOYON BAYANKU DA COMMENTS NAKU, BAKI BA ZAI FASALTA MUKU IRIN DAAƊIN DA NAJI BA DA KALAR SOYAYYAR DA KUKA NUNA MIN NA GODE NA GODE KWARAI DA GASKE. HASSANA SALLAU(MAMAN MUNIFA): DOLE NA AMBACEKI DON KINA ƊAYA DAGA CIKIN WACCE TA BA NI GOYON BAYA A WANNAN TAFIYA ƊARI BISA ƊARI BAN TAƁA YIN PAGE DA BABU COMMENT NAKI BA NA GODE KWARAI ALLAH YA RAYA ZURI'A YA BAR ƘAUNA TSAKANIN KI DA ABBAN MUNIFA. FATIMA A MUHAMMAD: SIRIKA KUMA AMINIYAR ANGO INA GODIYA DA GUDUMAWARKI KWARAI DA GASKE. ALLAH YA BAR ZUMUNCI YA NUNA MANA RANAR DA ZA MU ZO SHAGALI KADUNA. SIS NANAHALIMA KWARAI NA GODE DA GUDUMAWARKI ALLAH YA BAR ZUMUNCI. HANIFA MUHAMMAD GURIN: YAYATA KUMA AMINIYATA KAWAR CIN MUSHE NA. MY SHAYLAAA%% MY RIDE OR DIE🥰🥰NA GODE DA TAKI GUDUMAWAR DA SHAWARWARI AKAN KO WANI PAGE DA ZAN RUBUTA. SAFIYA GALADANCHI: ƘAWATA MATAR HAMMANMU FATAN ALKHAIRI ALLAH YA KAWO MANA KE KASAR FOMBINA💃💃 OUM AMEER: MASOYIYATA KWARAI NA GODE DA ƘARFAFA GWIWA ALLAH YA BAR ƘAUNA YA RAYA MANA SU AMEER YA KAWO WASU 'YAN UKU SAU UKU☺️ DA MA DUK WAENDA BAN KIRA SUNA BA NA GODE SOSSAI DA SOSSAI, TAKU HAR KULLUM 🖤GUREENJOH🖤