FEERYAL *Littafin kud'i ne ki-ka biya kud'i ki-ka karanta cikin aminci, FEERYAL mallaki na ne ni RASHEEDAT S DIRECTOR* Ki-ka saka 500 ta cikin wannan a account d'inπŸ‘‰πŸ»3170524141 Rashida Salihu first bank. sannan ki tura shaidar biya ta Whatsapp number taπŸ‘‰πŸ»08034690723 "Bissmilahi Rahmanurrahim" Wani irin mummunan sarawa kanta yayi tamkar zai rabe gida biyu. dasauri tajuya jikinta nabari tana fad'in "Ammie Ammie karkishiga bayi nan akwai wani abu!." ganin Ammie bata d'akin tanufi falo da gudu tana cigaba da kwalamata kira "Ammie! Ammie!!." Aunty data koma kitchen duba girki tafito dasauri dan jin kiran datake kwalamata da karfi. take fadin Ammie karkishiga bandakin. kafin ta rufa baki tawani irin rid'uwa akasa. tamkar an d'agatane aka bugata da kasa. tawani kwalla uban qara me rikitarwa. Aunty tayi kanta dasauri tana fad'in "Ke Feeryal lafiya mekika gani a bayin meye a cikin bayin?." takai hannu tana kokarin d'ago ta. Feeryal tawani irin dago kanta tareda yamutsa gashin kanta ta girgiza kan. tayi wani irin mikewa tsaye tabubbuga kafafunta a kasa. saida ilahirin cikin falon yadauki sautin bubbuga kafafun da tayi. kana tagyara tsayuwanta gijim kamar an aje abu mai matukar nauyi. bashiri Aunty tayi baya atsorace ganin yanayinta daya canza gaba d'aya. cikin wani irin murya me rikitarwa take fad'in "Tun da ta b'ata mana shiri to yazamo dole mudauki mataki akanta, dole mutafi da ita muje mu yasar da ita acan inda babu wani bil'adam d'in da ke rayuwa a gurin, wannan shine hukun cin da ya da ce da ita." Tayi wani irin juyawa tarufa aguje tayi waje da gudu, Aunty tabi bayanta da gudu tana kwallamata kira, tuni Feeryal tayi bakin gate ganin tana kokarin fita daga site d'in gaba d'aya. hankalin Aunty ya yi mugun tashi tana fad'in "Dan Allah kuyi hakuri karkubari dan Allah tafita a haka, ku tsaya ku fad'i me kuke bukata, kada ku wahalar da ita ku d'auki hakkin ta." tuni ta fice daga side d'in. Aunty tabita a kid'ime hankali tashe ganin babu wani sutura ajikinta daga ita sai towel dake daure a kirjinta. A guje ta d'aun hanyar babban get, Aunty na binta tana kira da kururuwan niman agaji a tare mata ita kada a bari ta fice a gidan gaba d'aya. Ajmal Zaraddin Shamsuddin Faisal. da suke hango abin da ke faruwa daga saman benen sashin su, dukan suka sauko suka fice daga sashin nasu, dai-dai san da Feeryal ta iso zata wuce get d'in sashin nasu. Zaraddin ya shige gaba da sauri ya yi saurin rukota ya rungumeta gaba d'aya a jikinsa, yawani irin jan numfashi san da yaji d'umin jikin ta da tattausar fatar jikin ta mai d'umi da laushi da tsamtsi a cikin jikinsa. ya kifa tafin hannunsa da kyau a bayanta yana dad'a matseta a jikin sa. Wani irin haniniya tayi tayi jifa da shi can gefe sai da ya had'u da jikin get gau! kake ji, ya zube kasa warwas yana gantsarewa da rike bayan sa. ta kuma zurawa a guje. Aunty ta sa hannu a kai tana fad'in "Innalillahi wa inna'ilaihirraji'un Ajmal Shamduddin Faisal dan Allah kada ku bari ta fita, ku kamo ta ba a hayyacin ta take ba." suka rufa mata maya da gudu, dukansu suka rirrije ta. sunyi-sunyi su iya janyota sun gagara raba kafarta da kasa. suka daddage da karfin su irin na matasa masu jini a jika, suka kuma janyo ta. da tayi wani irin ihu mai had'e da gurnani tayi haniniya da su duk ta wasar da su kasa. ta kuma rufawa a guje. Ihu Aunty ta fashe da shi hawaye na zuba a idon ta fad'i take "Ya Allah ka kawo min d'auki ka taimaka min ka taimakawa wancan baiwar taka da bataji ba bata gani ba, ya Allah ka hanasu cimma burin su a kan ta, dan Allah security kar ku barta ta fita ku tare ta dan Allah, innalillahi wa inna'ilaihirraji'un." Wani irin karo tayi tayi baya tangal-tangal kamar zata kife kasa sai kuma ta dawo ta tsaya daram. tana wani huci kamar kububuwa, tsaki yaja yana kallon wayarsa da ta fad'i kasa, fitowar sa daga sashin Mommy ke nan yana tafe idanunsa a kan waya baya kallon gaban sa, ba zato yaji ya yi karo da abu. bai d'ago ba idanun sa a kasa inda wayarsa take yashe kusa da kafafun ta, ransa a b'ace ya bi kafar nata da da kallo ganin ba'a d'au wayar an mika masa ba, kuma ba'ayi magana ba bare a bashi hakuri. yad'an surawa fararen kafafunta, tuf-tuf da su masu dauke da zarazaran yatso, sam kalar kafar batayi kama data kannen sa ba, duk da baya yawan zama da su amma yasan babu mai wannan suffar a cikin su. har sannan bai d'ago ba yana zaman jiran a d'auko wayar a mika masa, a fusace ya d'ago kansa. baiga fuskar da ke tsaye a gabansa ba, sakamakon gashin kanta da ke baze ya rufa mata fuska. a hankali tayi baya da kafarta d'aya ta d'aga d'ayar zata sa gudu. da karfi Aunty ta ce "Abdurrahi ka rike ta dan Allah kada ka barta ta gudu dan Allah!." Da sauri ya mika hannu ya fizgota dan tuni ta d'aga kafa ta sa gudu. ya dawo da ita ta garu da jikin sa. wani irin garuwa tayi garam tayi baya tana wani irin gurnani. cikin wani irin murya take fad'in "He kana da kwari, jiki kamar doki." ta kuma d'aga kafa zata sa gudu. a fusace ya kuma fizgota, tayi wani irin tirjewa, cikin matukar mamaki ya d'ago ya dube ta, jin yadda ta tike, kuma wai macece gatanan yar qarama agaban sa, to ko ba mace bace saboda yanayin sautin muryata da yaji tayi magana da shi amon sauti me rikitarwa har lau fuskarta rufe yake da gashin kanta. Tsayuwar sa ya gyara ya kai d'aya hannunsa ya ruko nata d'ayan yazamo duk yana rike da hannayen nata, ya janyo ta da karfi, tana tirjewa yana janta yakawota inda su Aunty suke , yana zuwa gurin yaturata wa Auntyn Aunty ta ce "Dan Allah Abdurrahim ka taimaka ka kaimin ita site d'ina zasu gudu da ita ne." yadube su Ajmal da suke tsaye cirko cirko kowannansu na dafe da inda yabuga. ya ce "Ku kamata ku kaita ciki." Ajmal ya ce "Ya Abdurrahim wlhy bazamu iyaba zubar damu tayi dukkanmu." gajeren tsaki yaja yakuma fizgo ta tana kokarin kuma gudu, yajanyota ya nufi sited'in Aunty aransa yake fadin "Wai harda mahaukatane a gidan yanzu." Aunty dake biye dasu jikinta nab'ari suka wuce har falo ya ya angiza ta a saman kujera, tafasa wani uban kara tana fadin "Sai mun tafi da ita tunda ta batamana shiri bazamu rabu da ita ba." takuma yunkurawa Aunty tafashe da kuka tana fadin "Dan Allah dan Annabi kuyi wa girman Allah ku kyale yarinyarnan, Abdurrahim ka taimakeni karkabari su tafi da ita ba ita bace Aljanune karkabari sutafi da ita. itako junkurawa ta kuma tawani irin shekewa da dariya tana fad'in Ba zai iya damuba dole saimun tafi da ita, tun da ta b'a mana shiri ni bakin aljani bana aike ya fad'i a banza, hahahaha." tadaga kafa tana kokarin guduwa. yasamata kafa tafad'i kasa rif ta wani irin yunkuri tamike tsaye, ta kai hannu takunce towel jikinta ta tayi jifa da shi, tana kokarin cire bra'n jikinta tana wani irin mummunar dariya HAHaHaHa. Aunty ta sa kuka tana fadin "Innalillahi wa innailaihirraji'un kuwasu irin shaid'anune zakusata tayi tsirara haba kukuwa, baku da imani da tsoron Allah ne." wani irin runtse ido Abdurrahim yyi cikin takaici da kosawa ya zabga mata wani mummunar marin da saida takife kasa tana wani irin gurnanani. Aunty dasauri tadauki towel din tarufemata a jikinta. Yazauna kan kujerar da take kife a gaban sa tare da d'agota daga kifen da take yazaunar da ita a kasa. ya saka hannu ya damko gashin kanta da karfi tare da gyara zamansa yasoma karanto ayoyin alkur'ani yana tofa mata, cikin zazzakar murya tamkar balaraben asali. ihu ta soma tana fad'in "Ka daina kona mu kai hatsabibine, ka cire hannunka a jikin mu kana da mugun dafi wane ne kai haka, zamu waiwayo ta kanka zamuyi bincike a kanka kai dafi ne ka kyale mu ka dai na kona mu zamu fitaaaa zamu fitaaa." bai sakaita da karatun ba har sai da ta sulale kasa tana birgima da shure-shure, da rantse-rantsen yanzun nan zai tafi har a bada." Ta jera wasu tagwajen atishawa,tana mikewa da kakkalmashe jikin ta, nan take tayi flat a kasa, tana sauke numfashi. Aunty rayi kanta da sauri tana dad'a rufe mata jikinta, da kiran sunan ta. "Feeryal Feeryal ke ce tashi Feeryal, nagode Abdurrahim." Baiyi magana ba ya mike tsaye ya fice daga parlour'n.......! Sai kunyi hakuri fa.... Mommy'n Twins ce Waziri kutub ya zube kasa bisa gwuiwowinsa, jiki na rawa idanunsa akan ruwan madubin ganin zahiri daga rayuwar Feeryal. ya ce "Ya shugaba na! shin mene ne da lilin da yasa ka hanamu bayyana domin kai mata d'oki cikin gaggawa? ta fuskanci azabebben wahala daga bakin aljani, kayi mana izini mu cimmasa." sarki aljani Matip ya gyara zamansa sannan ya ce "Kariyar da yafi naku ya tinkaro gareta, tabbacin da ke garesa shi ya sa na dakatar daku, shi d'in sulke ne garkuwar yaki, kuje ku cimma bakin aljani ku taho da shi a tsare shi." "Mun karb'i izini ya shugaba na." nan take waziri Kutup ya umurci dakaru uku da su je su taho da bakin aljani, dake can yana jinyar jikin sa da ke a babbake, batare da b'ata lokaci ba suka taho da shi aka tsare shi a kurkuku, tare da horo mai tsanani. Tuni gidan ya d'auki labarin aljanu sun tashi a kan Feeryal,yan kai kawo masu yayata batun sunata fad'in karya da gaskiya harda masu cewa Feeryal tsirara tafita, babu komai a jikin ta. Hankali tashe Ammah da Miemie suka nufi sashin Aunty. har lokacin Feeryal na kwance flat a tsakiyar parlour Aunty na ta tofa mata addu'o'i, tana yi tana hawaye. Ammah ta karaso da sauri ta ce "Kamata mu kaita d'aki Hajiya Fatima." Aunty ta mike tana share kwalla suka kinkimeta suka shige da ita d'akin ta. Miemie ta biyo su tana hawaye cike da tausayin Feeryal. a kan gado suka kwantar da ita. Ammah ta ja blanket ta rufe ta, tana fad'in "Sun sauka fa bacci take yi." Aunty ta gyad'a kai jiki a sanyaye. Miemie ta zauna kusa da ita tana sharar kwalla. duk tausayin Feeryal ya cikata. Ammah tayi ta karfafa Aunty, sai ana kiran sallar magriba kafin ta tafi, har lokacin kuwa Feeryal bata farkaba. Miemie kam tananan suna tare da Aunty a d'akin har wajen karfe 10 na dare kafin Feeryal ta farka. da taimakon su tayi wanka ta sa kaya har ta d'an tab'a abinci. sai wajen 11 Miemie ta koma sashin su. Washegari. Hajiya ce zaune gefenta Abdurrahim ne zaune yana dan kishingid'e idanunsa a lumshe, tun da ya shigo gaishe ta Hajiya ta tsare shi da batun wai ta sami labarin shi ya tsare Feeryal bayan da kowa ya kasa riketa. Hajiya ta bubbugashi tana fad'in "Kai abokin turawa yanaganka haka kamar mara lafiya, dama ina kai ina fad'a da aljanu bare yarinyar ma da ita kanta aljanace, salon kaje taro su sushige maka jiki, waya sani ma ko sun shige ka, ina da wani ajiyayyen hayaki bari na d'auko kayi." a hankali yabud'e lumsassun idanunsa ya mike zaune yana jan d'an gajeren tsaki, Hajiya ta ce "In banda hali irin na Fatima daga isowarka kasar ko hutawa ba'a bari kayi ba a wani had'aka da kama aljana, in ba mugunta ta so kulla wa ba, bari naje na d'auko hayakin nan nayi maka, haba dan Allah mugunta kiri-kiri mutane sun iya shi, Allah kad'ai yasan wasu irin aljanu ne suka shiga jikinka." Hajiya na kokarin mikewa shi ya rigata. yatashi yasaka takalmansa yyi ficewarsa. Hajiya tadaga murya tana fad'in "Kai abokin turawa kaji iya shege ka tsaya ayi maka hayakin a kora maka su, shine zaka tafi, bari naje na sami Daddy'n ku, wlh ba'a isa a salwantar min da rayuwar jikana na fari ba, ina dalili ina mafari." Daf da zai shiga shashinsa saiga kiran mommy yashigo wayarsa, yajuya yanufi shashinta yana shiga yagaisheta, ta amsa a dabarbarce tana fad'in "Abdurrahim ina ce dai lafiya bbu inda kaji ciwo? meya kaika da fad'a da aljanu alhalin yarinyarma ita kanta aljanace, to karnasake jin kashiga sabgar yarinyar nan inma mutuwa zatayi ta mutu ba abinda yadameka, ta fita zata tafi gun danginta aljanu in da ta fito ina ruwan ka da tsare ta, imma Hajiya Fatima ce ta ce ka tsaro mata ita, to ban yadda ba kar na sake ji, dan in ba kasa sani ba ka sani, yarinyar aljana ce d'auko ta tayi a cikin ruwa babu kalar fitinar da bata haifar ba, da kage ganin ta yanzu haka fitina ta haifo musu a can Abuja gidan iyayen Hajiya Fatima'n, shine aka dawo da ita nan mu ta karasa mu, shine suka fara daga kanka, tun da sunsan kaine magajin gidan, suke so su san yadda zasuyi su sabautar da rayuwar ka." Baki yatabe cike da kosawa da maganganunsu shi an dameshi da maganan da bai shafeshiba, dan kawai ya taro ta sai abi ayi ta damin shi ana cika masa kunne da wasu maganganu, to meye damuwar sa shi, imma aljanar ce sai tayi aljanancin ta. batare da ya ce da ita komai ba yanemi waje yazauna akan kujera. ya ce " mommy ina abinchi?." ta ce "Ba nasa a Ameerah ta kai maka." "Babu wani sai wanda masu aiki sukayi?." dubansa tayi har yanzu dai d'abi'ar sa nanan na kin cin abincin masu aiki, wannan gadon da ya yi na Daddy da kakan sa yana b'ata mata rai. ta ce "Babu duk masu aiki ne suka girka, to wai meye ne abincin masu aikin yake yi, manyan ma'aikatan hotel kwararru a fannin girki su ke girki a gidan nan, meye aibun abincin su, acan waye yake maka girki ba mata kake da ita ba ina masu aikin ne." bai yi magana ba ya mike ya yi waje. Tun da sassafe Miemie tashigo shashin Aunty a falo ta tadda Aunty tana aiki, ta gaisheta tana tambayanta yaya feeryal da jiki Aunty ta ce "Dasauki tana daki ma tana bacci haryanzu." Miemie ta ce "Ammah ta ce na gaishe ki da jikin ta, bari na duba ta." "To jice da ita jiki da sauki." ta ce tom. tashige d'akin Feeryal tasameta tana bacci acikin bargo. tazauna a gefenta tana kallon kyakkyawan fuskar ta da yi wasai, a hankali ta ke sauke numfashi. cike da tausayin ta Miemie ke kallon ta. takai awa daya da shigowa d'akin kafin Feeryal tafarka. tamike da murmushi tana fad'in "Miemie yaushe kikazo?." "Tun d'azu nazo nashigo kina bacci." "Shine baki tashe ni ba." "Uhm-uhm kiyi baccin dai, Ammah tace a bacci akafi samun sauki." Feeryal ta kuma murmushi tazamo bakin gado tana fad'in "Kawai naji bani da lafiya bansan me ke dami na ba, ina dai jin bana jin dad'in jiki na, bari nayi wanka Miemie, ko zan ji na d'an ware." tana mikewa da sauri ta koma ta zauna bakin gado tana fad'in "Wash!." da sauri Miemie ta ce "Ya ya dai Feeryal?." "Ciwo jikina yake min Miemie, gwuiwa ta ciwo yake min, Miemie ta ce "Sannu Allah yasauwaka yi wankan muje ki karya." Miemie nazaune hartayi wankan tafito tashirya cikin dogon rigan material mara nauyi. suka fito falo suka tadda Aunty tagama shirya breakfast. ta had'asu akan dinnig, suka haye dinning tare sukayi breakfast har da Aunty. Feeryal sai yamutsa fuska take tana fad'in wash nan d'inta namata ciwo, can na mata ciwo. Aunty da Miemie sai sannu sukeyi mata, Aunty ta ce "Bari nasa a kawo miki magani ko azo amiki allura ne kawai zakifi jin dad'i." dasauri taware ido cike da jin tsoro tana fad'in "Ah ah Ammie karkisa ayimin allura abani maganin kawai." Aunty ta ce shikenan "Maganin kawai za'a kawo miki." Aunty takira family doctor d'insu ya kawo mata magani. Har azahar Miemie sunatare da Feeryal ashashin Aunty. kafin takoma sashinsu tana shiga taga Faisal zaune Ammah tana d'uma mishi hanunsa da ruwan zafi. sai wani raki yakeyi yana fad'in "Ash wlhy Ammah dazafi anya ba tsagewar kashi ba ce kuwa." Miemie ta karaso tana zauna kusa da su tana leko fuskarsa tana dariya. "Kai Ya Faisal wlh kana da raki, sai kace kariya kayi, d'an bigewa ne fa." hararar ta ya yi ya ce "Ke wlh ni tunani ma nakw kamar kariyar ce, dubi fa hanuna inda ya kumbura." Ammah ta ce "Kai da'alla tafi can kariyar ce har zaka iya kwana da ita." ya ce "Allah Ammah hannnun nan fa tayi tsami sosai daurewa kawai nake, wlh wannan bugun badai mutum ba sai dai aljani, wlh Ammah in kin ga yadda ta wujijjigamu ni da Ajmal da Shamsuddin kyace jarirai ta d'auka tayi jifa da su, dama Zaraddin kam na kasa shi aka fara bugawa da kasa." Miemie ta tuntsure da dariya har tana rike ciki cikin muryar dariya take fad'in "Lallai kunji hannun mazajen aljanu, haba ai wannan abin kunya ne ace dukanku hud'u kun kasa iya rike aljani d'aya, gaskiya kun bada maza." "Ke dalla tafi can in da Feeryal d'in ce ba mahaukatan aljanun da suka zo kanta ba, wanda naushi d'aya nayi wa yarinyar can wlh sai ta suma." "Ba waninnan kun dai kasa." Miemie ta fad'a tana kuma shekewa da dariya. Faisal ya kai mata bugu da d'aya hannunsa yana fad'in "Ke ni sa'an ki ne, mutum uku sakanin mu kafin ke kar kiga basa nan ki d'auka ke kike bina, Ammah ki gaya mata wlh zan b'alla ta a nan." Miemie ta mike da gudu tayi kofa tana cigaba da dariyar ta ce "Bari naje naga su Ya Ajmal da Shamsuddin da Ya Zaraddin ko wani hali suke ciki ko kafarsu ce aka b'alla musu su, Allah ya taimake ku ma da ya turo muku Ya Abdurrahim, badun haka ba kam sai asibiti." "Zan rike ki Miemie na rantse sai na fasa miki baki." tuni tayi waje tana dariya. Sashin Mom ta nufa ta tadda Zaraddin kwance ga magunguna a gefen sa, Shamsuddin kuma na zaune. ta karaso tana kunshe dariyar ta da fad'in "Sannun ku Ya Zaraddin Ya Shamsuddin ya jikin naku." Sahla ta yi caraf ta ce "Ai wlh shegiyar mayyar aljamar nan sai ta bar gidan nan." Zaraddin ya d'ago da sauri ya ce "Ina ruwan ki, babu in da zataje tana nan." baki ta tura tana kunkuni. shiko ido ya lumshe babu abin da yake masa yawo cikin ido da kwakwalwa sai suffar Feeryal da tattausar jikin ta, sai wani shigewa cikin kujera yake yana ji kamar tana cikin kijin sa. Miemie ta fashe da dariya tana fad'in "Wai Ya Zaraddin duk bugun da kuka sha ne haka kamar fa ko iya tashi baka yi, gadai Ya Shamsuddin shi dai kamar nashi da sauki, lallai kunji jiki kunji ta maza." ganin hararar da suke mata tamike ta gudu tayi waje. ko da taje sashin Mommy bata sami Ajmal ba, Ameerah ta ce mata yafita a mota. Satin Feeryal guda bata fita ko nan da can kullum Miemie na hanyar zuwa dubata. suna zaune a d'akin Feeryal suna hira Miemie ta ce "Uhm bari natashi naje Ammah ta ce naje nakira Ya Faisal, takira wayansa bai d'agaba yazo yashafa maganinsa." Feeryal ta ce "Ya Faisal d'in bashida lafiya ne?." dariya Miemie tafashe dashi ta ce "Ai bashi kad'aiba harda Ya Ajmal Ya Zaraddin da Ya Shamsuddin, ammafa sun warke kawai Ammah ce wai sai an yi ta binshi yazo ya shafa magani, kaman wani karamin yaro, targad'e yayi a hannu." Feeryal tawani waro ido ta ce "kai Miemie kefa muguwa ce shine kike dariya Accident sukayine?." Miemie takuma kwashewa da dariya ta ce "Karo sukayi da Aljani." Feeryal takuma ware ido tana fad'in "Aljani kuma a'ina suka sami aljani kuma?." Miemie ta ce "Ke dalla duk kin wani tsorata aljanin kanki mana." ta ce "Ni kuma!." Feeryal ta fad'a tana buga kirji. Miemie ta ce "Sati guda kenan da sukayi karo da aljanun kanki dukkansu sai da sukaji ajikinsu." nan da nan Feeryal tashiga wani yanayi tana fadin "Aljani kuma ni d'in harkuma sukaji rauni? ina na fitama Miemie nida banida lafiya, ina kwance kemafa kinsani, ko ke ma kin yadda ni aljanar ce." nan da nan idanunta ya kawo kwalla. Miemie ta ce "Ke dalla karki d'aga hankalinki na tunasune abin ya bani dariya." Feeryal ta ce "Dan Allah kibasu haquri ni bansani ba." ganin kamar hankalin Feeryal d'in ya tashi ta ce "Ke dalla wasa nake miki, bashida lafiya ne kawai." Miemie hartafita tana dariyar mugunta. Washegari Feeryal tafita taje sashin Ammah dan taji sauki sosai. bata sami Miemie ba sai Ammah ita kad'ai, Ammah take Fad'a mata Miemie tana sashin Hajiya. Feeryal ta fita. harzata koma sashinsu sai tajuya tanason ganin Miemie. a hankali nufi sashin Hajiya tashige ciki tana waige-waige dan tasan sashi Hajiya akwai mage. ahankali take takowa har ta iso bakin kofar falo, d'an tsayuwa tayi. tuno da kashedin Hajiya akan karta kuskura tashigo sashinta. d'an jim tayi da tunanin ko ta koma ne, sai kuma ta dan leko kanta, tana fatan ta hango Miemie ta kirata da hanu. karaf suka hada ido da hajiya. Hajiya ta saki tana fad'in "Au har nan kika biyo shi, kinzo ki karasa shiga jikin nasa ke nan? jikan nawa kika biyomin jika kina lekensa ki samu ki karasa shiga jikin sa, shigo munafuka zo nan aljanar banza." Hajiya ta yafato ta da hannu. Abdurrahim yana zaune idonsa yana kan wayar dake hannunsa yana dannawa. gefen sa abokin sa ne Dr Imran yana cin abinchi. A hankali ta tako cikin parlour'n jiki a sanyaye, tazo gaban ta ta tsaya kanta a kasa tana murza 'yan yatsunta. Imran ya d'ago yana duban wanda Hajiya take wa fad'a. da d'an mamaki yake kallonta, yaga kaman yasan yarinyar da Hajiyan take wa fad'a. Hajiya ta zazzare mata ido "Na ce kin biyoshi harnan kikarasa shiga jikinsa ne, munafuka bance kada ki kuskura ki tako min cikin sashi ba, kuma nayi miki kashedi kan jikoki na, bance kads ki shiga tsafgar wani daga cikin su ba, shine kika biyo shi dan ki karasa shiga jikin sa ko." kai ta girgiza da sauri idanunta suka kawo kwalla, muryarta na rawa ta ce "Gurin Miemie na zo." ta ce "Fita ki bani guri munafukar baza aljana kawai." ai da gudu Feeryal ta fita, bata tsaya ba sai da ta fice daga sashin nata gaba d'aya. Miemie ta b'ata rai taji haushin abin da Hajiya ta mata, sai dai bata da bakin magana yanzu duba da wanda yake gurin. har ta fice Abdurrahim bai d'ago ba idanunsa yana kan waya. Tana fita Imran ya aje jokali da sauri ya dubi Hajiya ya ce "Hajiya da gaske aljana ce wannan?." Hajiya ta nimi guri tazauna tana cewa "kwarai kuwa Imrana yarinyar nan Aljanace na gaske, kar kaga abin da ta mana a lokacin auren Farida, da manyan zakuna ta zo ta wargaza taron jama'a, in ba aljana ba ta ya za'ayi ta d'auko zakuna tana yawo da su." Imran ya gwalalo ido cike da tsoro ya ce "Innalillahi amma Hajiya karfa ta fita ta dawo mana da damisai, A.A ana magana kana shiru, yarinyar da kayi jinyarta a Abuja ce fa, wai ma ya akayi tazo gidan nan, dama wancan karon naga Daddy a asibitin da ma tana da dangi da gidan nan ne?." Hajiya ta ce "Dangi da wa? tsintacciyar tsintarta Fatima tayi a cikin ruwa, d'iyar aljanu ce fa, kai tunda kake katab'a ganin kyakkyawa irin ta ai sai aljanun ruwan." Imran ya kama baki yana saurarar Hajiya. Abdurrahim yaja gajeren tsaki ya mike yanufi kofa. Imran ya biyo bayan sa, Hajiya tana fad'in "Kai abokin turawa ina zaka je, ka tsaya naje na duba kar ta tsaya a hanya tayi maka wani abin, kai Imrana kasashi kuyi addu'a wasayyawu ya tsaya a kanta." Imran ya ce "To Hajiya A.A ka tsaya kadai ji abin da Hajiya ta fad'a." ganin ba tsaya wa zaiyi ba ya biyo sa da sauri. Feeryal da Miemie suna tsaye a d'an gaban sashin Hajiya. Miemie nata bata hakuri sai share hawaue take. Feeryal na d'agowa sukayi ido biyu da Imran. da sauri ta ce "Miemie mu tafi." Imran kuwa suna had'a ido da sauri ya makale bayan Abdurrahim cikin yin kasa da murya ya ce "A.A gata nan fa mu canza hanya." Abdurrahim baiyi magana ba yaci gaba da tafiyar sa. sai da suka zo daf da su sannan yaja ya tsaya, ya d'an dubeta a dakile ya ce "Wai ke aljana ko......! Mommy Twins ce Da sauri ta d'ago idanunsu ya sarkafu da juna, cikin hanzari ta janye idanun ta, ya yin da taji wani irin mummunar fad'uwar gaba. kwarjinin sa ya mata mugun girma ta iya jona idanun ta cikin nasa. a hankali tayi kasa da kanta jikin ta, a matukar sanyaye. tsintar kanta tayi da jan d'an gajeren tsaki a kan lab'b'anta, wan da batayi sammanin fitowarsa ba. ta gyad'a masa kai ta ce "Eh." har lau kanta a sunkuye. kai ya jinjina idanunsa a kanta. sai kuma ya soma tafiya batare da ya kuma cewa komai ba. Miemie tayi saurin janyo hannunta suka nufi sashin Aunty. da sauri Imran da yagama tsorata ya biyo sa. ya sha gaban sa murya a marairaice ya ce "A.A kasan me kayi kuwa? dan Allah dan annabi ka rufa mana asiri, dan nasan idan ta tashi ba iya kanka zata tsaya ba, har da ni da ta ganmu tare, meyasa kayi mata irin wannan tambayar, haba A.A, meye na tambayar ta ita aljana ce, kagafa ranta ya b'aci; wlh babu ruwana ni zanje na bata hakuri tun kafin ranta ya dad'a b'aci." "Kai dalla ka dame ni bani hanya na wuce." "Wai kai A.A kayi abu ma bakasan kayi ba, wani iri ne kai da baka da tsoro ne haka, to wlh ni kam babu ruwana bazaka jamin fitina ba ina zaman zama ta." ko oho ya yi masa har suka shige side d'in sa. Imran kuwa gaba d'aya ya rud'e bai fasa masa magana ba. Sai da su Feeryal suka shige sashin Aunty kafin Miemie ta tsayar da ita a farfajiyar side d'in. Miemie ta wawwaro ido ta ce "Feeryal me yasa zaki ce masa haka ki amsa masa ke aljana ce, kinsan waye shi a gidan nan kuwa? dan Allah ki rufa mana asiri, tsaki fa kika yi masa kin san kuwa Ya Abdurrahim baya son tsaki." "Ya zanyi Miemie shike nan tun da Allah ya halicceni haka laifina ne, idan ban amsa masa cewa ni d'in aljanar bace me kike so na ce masa, bayan kowa da hakan yake kira na, mayyar aljana annoba." hawaye suka fara zuba a idon ta, ta rike hannun Miemie gam cikin muryar da kuka ke son kwace mata ta ce "Miemie duk wanda ya kuma tambaya ta ni aljana ce haka zan amsa masa, illa iyaka ina suce na bar musu gidan su." Miemie ta ce "Feeryal kinyi ganganci masa tsaki kuma yaji fa." "Nasan yaji ai ni ma haushi tambayar tasa ta bani." Miemie tasa hanu a kai ta ce "Nashiga uku bansan ya zan yi ba yau dole zamuje ki bashi hakuri, Feeryal ni ina son jiki na bana son abinda zai tab'a min lafiyar jiki, Feeryal yaushe kika iya maida magana haka? ina zuwa." ta fad'a da sauri ta juya ta fita. Feeryal ko mai da hawayen idanun tayi, taja kafa ta shige ciki. Aunty na ganin yanayin ta ta ruko hannunta tana tambayar ta me ke faruwa. raurau tayi da idanun sai kuma ta cuno baki gaba ta ce "Ba wani ne ya tambayene wai ni aljana ce ko." tayi kwafa "Ai na rantse idan ya sake ce min bazan kyale shi ba." Aunty ta kura mata ido ta ce "Wani waye a ina kika ganshi?." "Daga sashin Hajiya ya fito Miemie ta ce min wai shima yayan su ne." Aunty ta buga kirji ta ce "Ba dai Abdurrahim ba kirufamin asiri Feeryal kira bani da Hajiya, daki tab'ashi gara ki tab'a kowa a gidanan nan, dan wallahi akansa Hajiya bata kyale kowaba babu ruwanki dashi." Feeryal tawuce d'aki tana shagwab'e fuska. babu wanda yatab'a tareta haka gaba da gaba yana yimata irin tambayar da ya yi mata. Tana shiga ta saki murmushi ganin wad'anda suke cikin dakin. ta ce "Lah chuchu chulu yaushe kukazo" sukace mata tund'azu muke jiranki. ta ce "Dana sani da tundazu nadawo gurin Miemie naje." sukace kinason mudaumiki mataki akanshi ne?. kai ta gyad'a ta ce "Eh amma fa karkuyi Ammie'nah ta sani dan ta ce babu ruwa na da shi." sukace to. zama tayi suka soma hira sosai daga bisani, ta ce zatayi wanka. tashige bayi sukuma suka tafi. bayan tagama wanka tafito ta gansu a tsaye kowannesu rike da hannunsa. murmushi tayi musu ta ce "Kunje kun same shi?." sukace mata "Eh kai ina wannan fa bazai tab'uba, munkasa iya masa komai, sai dai mubaki wani abu ke kimasa da kanki, mun mun kasa iya matsowa kusa da shi bare har mu tab'a shi." Chuchu tasa hannunta abaya taciro wani abu ta mika mata ta ce "Kisan yadda za'ayi yataba jikinsa." Feeryal taware ido ta ce "Zan iya kuwa abarshi kawai." sukace zaki iya mana jikinshi kawai zai tab'a shikenan kin rama abunda yayi miki. takarba tabude drower tasaka tadawo suka cigaba da hirar su. Da sauri Umma Karima ta nufi sashin Mommy. ta jata suka shige can kuryar d'aki. Mommy ta dube ta tana zama bakin gado ta ce "Allah dai yasa lafiya Hajiya Karima, irin wannan shigowa a bujajan haka." "Inako lafiya Hajiya Halima, kwana uku boka Mali ya bani zai turo bakin aljani ya gama da waccan matsiyaciyar juyar, kusan kwana goma ke nan nake zuba ido naji shiru, ba na fad'a miki yadda mukayi da shi ba." Mommy ta ce "To ni ma dai har yanzu ban ga alamun hauka a jikin ta ba, to ko watakila bai gama aikin bane, amma kinsan maganar boka Mali baya fad'u kasa." Umma Karima ta ce "To ai nima shine na gani watakila bai gama aikin bane dan ya ce min aikin yana da wuya, sai anyiwa aljanin shiri, kai nifa kinsan bana son jira da yawa, nafi son komai cikin gaggawa; yau zan koma gurinsa kawai, naje naji mekefaruwa, in kina da aike ki kawo." Mommy ta ce "Ai kuwa ina da sako, batun auren yaron nan Abdurrahim da Kuraiba, jiya na tsare shi da batun tun da ya dawo ayi-ayi-ayi auren nan, mahaifiyar yarinyar nan kusan kullum sai ta kira ni, 'yar nan bata tab'a ganin sa ba sai a hoto amma ta ce taji ta gani sai shi, Hajiya Luba ta ce kullum sai ta taso ta gaba itafa shi take so a aura mata shi kawai har kuka take a kansa; amma yaron nan nayi ta binsa yaje gidan su yaki kin san sa da masifaffen taurin kai, ki fad'awa boka Mali ya karkatar da hankalinsa yaje su dai-dai ta ayi auren nan." Umma Karima taji wani dum a kirjinta amma sai ta waske ta yab'o murmushin yake a fuskarta ta ce "Ai kuwa in banda Abdurrahim me yake jira da bazai yi aure ba, to amma fa kinsan sai kin kawo kafin alkalami kafin a fara aiki." "Ah ai dama dole bari na baki wani abu ki bashi." ta mike taja drower ta d'au dubu d'ari biyar ta mika mata ta ce "A kai masa wannan idan ya ce da kari ba matsala za'a kara masa." Umma Karima ta karb'a ta mike tana fad'in "To bari naje duk yadda ake ciki zakiji." ta fice ta koma sashinta ta shirya ta garzaya dajin boka Mali. Umma Karima na zube a gaban boka bayan ta gama sanar masa da rashin nasarar su, har yanzu dai Hajiya Fatima na nan daram babu abin da ya same ta. tana zaune ta kasa kunne tana jin jawaban boka Mali cikin b'acin rai yake fad'in "Mun tura bakin aljani sai dai anyi rashin sa'a, basuyi ido da ido da ita ba; alamu na nuna mana wani ya haukace a madadin ta, sai dai abin bakinciki tun ranar nake zuba idon ganin bakin aljani da kyakkyawan labari, amma har yau bai waiwayo ni ba, wannan yarinyar da take rukonta hatsabibiya ce nayi tason ganin ta cikin duban tsafi na kasa, wannan yarinyar tana da had'ari dole sai ta kauce a gareta kafin a sami biyan bukata." ta ce "Boka babu yadda za'ayi a kawar da yarinyar ita?." ya ce "Ke zakiyi hakan idan kikayi mukuma zamu karasa sauran aikin, dan bama iya ganin ta a cikin duban tsafin mu." Umma Karima ta jinjina kai da tunani iri-iri a ranta. Umma Karima ce zaune a d'akinta ita da kanwarta Siyama, washegarin da ta je gurin boka Mali. ta sa Siyama tayi wanka ta shirya cikin wasu, d'amammun kaya wanda ya bayyana surar jikinta gaba d'aya. ta mikawa Siyama wani kwalli a cikin d'an tandu da kwalbar turare wanda boka Mali yabasu ta ce "Saka wannan kwallin a idon ki, ki shafa turaren a fuskarki, kud'in aikin da ta bayar ayiwa d'an ta a kan wata shi na bada ayi a kanki zuwa kan d'anta, Hajiya Halima ke nan har yanzu da sauran ki kar nake ganin ki, kin haifi 'ya'ya maza, a yau Alhaji ya fad'i ya mutu kin mallake gidan, tun da nayi-nayi ban samo d'a na miji ba, to ki sani akan d'anki zan samo d'a na miji, daga nan kuma zance ya kare." Siyama ta karb'i kwalbar turaren tana dariya ta shafa. tana fad'in "Sai dake Aunty na." Umma Karima ta ce "Yauwa to yanzu komai yayi dai-dai Abdurrahim yana ido biyu dake, shikenan burinmu yacika yanzu iwar haka yananan a sashin Hajiya Halima; jeki can in baki sameshiba ki garzaya sashinsa basaina gayamikiba ko me zakiyi kinsa meyakamata kiyi, d'an ta zai shigo hannun mu reshe zai juya da mujiya." Siyama tashige sashin mummy da sallama tana wani kararraya tazauna akan kujera inda ta taddasu Ameerah da Sumayya tagaida, mummy data fito daga bedroom d'in ta. Sumayya ta bita da kallo tana fad'in "Irin wannan kwalliya haka Aunty Siyama, ina zuwa haka?." "Kai Sumayya sai kace bana kwalli, babu inda zani." Sumayya ta yi dariya ta ce "Ai kwalliyar tayi kama da ta zuwa party ce." Ameerah ta kallete ta da wutsiyar ido, ta yamutsa fuska ta cigaba da dannan wayarta. Siyama ta ce "Wai Ameerah ba magana ne?." Ameerah ta d'an d'ago ta ce "Sorry hankali na na wani wajen." Siyama tayi shiru da bakin ta dan ta san halin Ameerah sarai bata kyale kowa ba. ta gyara zaman ta tana d'an satan kallon gun bata dai ganshiba. zuwa can ta mike ta fita. Tana sako kanta zata fice daga parlour Mommy sukayi kicub'us da shi yana kokarin shigowa. ta wani sake jiki tana wani yauki, ta narke murya "Barka da warhaka yallab'oi, ina yini." "Lafiya." ya amsa a takaice ko in da take bai kallaba ya rab'a gefen ta ya shige cikin parlour. wani irin lumshe idanu tayi tare da jan numfashi ta na shakar daddad'an kamshin sa. da sauri ta bud'e idanunta, ta taune baki tana dana sanin da ta fito da ta cigaba da zama har ya shigo. da sauri ta juyo ta koma ciki a zaune ta ganshi gefen Mommy. ta zo ta gaban shi ta wuce tans kad'a mazaunan ta, ta zauna kusa da Sumayya kujeran da ke fuskantar sa, Sumayya ta ce "Aunty Siyama baki tafi ba ashe." ta d'an saci kallon in da yake fatanta ya d'ago su had'a ido, shiko baima san tana yi ba idonsa akan waya. ta ce "Am Sumayya dama aron wayarki zaki bani nakira tawa bansan ina na jefa ta." Ameerah ta kalleta tana mara baki ta lura da satar kallon da take wa yayan nasu. "Yar wahala." ta fad'a a kasan ranta. Sumayya ta ce "Ina ma wayar tawa take." ta waiga gefe da gefen ta "Yauwa ga shi can." ta nuna kujerar da Abdurrahim ke zaune gefen sa wayar take, shigowar sa Sumayya ta tashi a kujerar ta bashi gurin zama kusa da Mommy. Sumayya na kokarin mikewa ta d'auko mata, tarigata mikewa. ta isa gurin ta kai hannu kamar zata d'au ka sai ta tura wayar ya da d'a matswa jikin sa. ta saka hanu ta gogi jikin sa. da sauri ya d'ago suka had'a ido, tawani narke murya "Oh yihakuri waya zan d'auka." gajeren tsaki yaja ya maida idanunsa kan waya. da sauri ta juya cike da farincin burin ta ya cika, tad'an lallasa wayar kana ta mikawa Sumayyar wayarta ta ce "Naji muryar Nabila wayar tana hannunta." ta juya da sauri ta fita cike da farin ciki. Tana komawa sashin su ta rungume Umma Karima tana fad'in "Aunty Karima ya ganni na ganshi." Umma Karima tayi makirin dariya ta ce "An gama 'yar gari, kwantar da hankalin ki kin sami Abdurrahim a tafin hannunki." suka wani kwashe da dariya suka tafa. Mommy ta dubi Abdurrahim da tun shigowar sa daya gaisheta bai kuma magana ba, sai aikin danna wayarsa ya ke. ta ce "Kaje kun gaisa da Kuraiba'n kuwa?." "Mommy abani breakfast." ido ta bisa da shi sarai tasan so yake ya kawar da maganar nata. ta ce "Ameerah je kice Shatu ta had'o masa breakfast." "No ki barshi." yafad'a tare da mike wa tsaye. Mommy ta ce "Ai nasan dama ba ci zakayi ba shiyasa ma ban sa an kaimaka ba, ina tayi maka magar yarinyar nan baka cewa komai." "Banje ba." ya fad'a a takaice Mommy ta ce "Amma ai yakamata ace kaje, ko da sau d'aya ne ku gana, kafin akai sadaki." ya zura takalman sa baiyi magana ba yafice. Sashin Aunty ya nufa dan yasan can ne kawai zai sami abincin da zaici cikin kwanciyar hankali. da sallama ya shigo Aunty na kokarin shiga kichin. ta dakata ya karaso suka gaisa, yanayin sa ya tabbatar mata da abinda ya kawo shi, dan tasan gadon Daddy ne ajikin sa, shima baya cin abincin masu aiki. Aunty tayi murmushi ta ce "Abdurrahim ka isa dinnin bari na kawo maka breakfast." ta wuce kichin shi kuma ya kara dinnin ya zauna kan d'aya daga cikin kujerun dinning d'in. ta had'o masa breakfast mai rai da lafiya ta kawo masa. kana ta koma kichin tacigaba da ayyukan ta. Feeryal ce kwance ke baccin ta cikin kwanciyar hankali, kiran wayar ta dake karkashin pillow da take kai yata da ita. mika tayi had'e da salati ta zura hannun ta karkashin pillow ta janyo wayar, batare da ta duba mai kiran nata ba ta kai wayar kunne idanunta a lumshe cikin muryar bacci ta ce "Hello." numfashi ya sauke mai sauti ya ce "Har na cire rai da picking call d'ina, Feeryal me yasa bakya d'aga wayata? i miss you Feeryal ko sau d'aya ki bani dama mana, hope kina lafiya." shiru tayi batayi magana ba, amma ta gane mai muryar. Major Sadam ya rumtse idanunsa yana jin sonta na zaga jini da jijiyar sa ya ce "Please Baby let me know kina sona." nan ma shiru tayi wayar tana kunnen ta. "Feeryal." ya kira sunan ta. a hankali ta maida idanunta ta lumshe tana saurarar sa, nanma shiru batayi magana ba. "Kinyi min izini anjima na kira ki bayan kin gama bacci?." a hankali ta bud'e idanunta cikin tsiririyar muryar ta ta ce "Eh." cikin matukar jin dad'in amsashi da tayi ya ce "Yes! thank you bye." Ta sauke wayar a kunnen ta, ta mike zaune tare da yin hamma, har yanzu bacci ne cike tam a idanunta, sai dai tana jin yunwa dan daren jiya bata ci ba ta kwanta. ta kalli agogo karfe 11 har da rabi. ta zame blanket d'in da ke rufe a jikin ta. ta zamo bakin gado ta mike ta nufi kofa ta fito, daga ita sai riga da wandon bacci pink masu samtsi. Tun daga bakin kofa ta ke fad'in "Ammie yunwa Ammie yunwa nake ji." a tsakir parlour ta tsaya tayi wani dogon mika mai had'e da hamma ta saki hannayen ta sharaf tana b'ata fuska ta cuno d'an karamin bakinta gaba cikin muryar shagwab'a tashiga bubbuga kafa a kasa wan da ilahirin jikin ta matsawa suke tana fad'in "Ammieeeee ina cake d'ina." ta nufi dinnin tana cigaba da kiran Ammien nata. Aunty ta fito daga kichin da sauri ganin ta nufi dinning tana mussuke ido da hannayen ta bata ma kallon gaban ta. Aunty ta ce "Ke Feeryal." cak ta tsaya bata kai ga karasawa dinning d'in ba. ta juyo tana tura baki da fad'in "Ammie yunwa nake ji." "Maza je ki canza kayan jikin ki sai kiyi wanka kizo." ta juya tana yarfe hannu cike da shagwab'a ta koma d'aki. A hankali ya tura plt d'in abincin ya mike, Aunty da ta fito daga kichin rike da wani had'ad'd'en kula, perpesun naman kaza ne dayaji kayan had'i na musamman acikin kular. ta ce "Har ka gama ne Abdurrahim?." ya ce "Eh nagama Aunty." "Dama na karo maka wannan ne to gashi ka tafi da shi." ta mika masa kular ya amsa tare da fad'in "Nagode." tayi murmushi, shiko ya juya ya fita.....! Mommyn Twins ce Da sauri Miemie ta shigo d'akin Feeryal ta isketa kwance tana aikin ta na buga game a waya. ta hayo gadon tana fad'in "Yanzu dama wayar nan tana hannun ki nake ta kira baki d'aga ba." fuska ta marairaice ta ce "Ayya Miemie wayar a nan na barta yanzu na shigo na d'auka." "Shine kin ga kira bazaki bi kiran ba." "Ai missed call d'in da yawa shine kawai ni ban duba ba." "To Allah ya shirye ki watarana sai arziki ya kira ki kin ki d'agawa ya wuce ki." dariya Feeryal ta yi ta ce "Yi hakuri to, ya akayi?." "Tun d'azu nake ta kiran ki nace miki ki shirya anjima zamuje, dinner yayar kawar mu, Safeenat Sa'id." "Ke da su wa da su Ameerah wai? ni kam bazanje ba kuje abin ku, kitaho min da tsaraba." Miemie ta harare ta ta ce "Ke kenan idan akace aje guri kice bazakije ba, kullum kina kunshe a gida a d'aki, ina ruwan ki da su Ameerah a kansu zaki zauna, yarinya tayi miki ne nagaya miki karki kuskura ki kyale ta, barina naje na fad'awa Aunty mun tabayi Daddy ya ce muje, idan ta ce kije kuma sai kin je." ta zamo a gadon da sauri tayi d'akin Aunty. Jim kad'an ta dawo ta ce "To wlh Aunty ta ce muje, bari ma na ciro miki kayan da zaki sa kifara shiri kafin nima naje na shirya, 8 za'a fara a tashi 11 bikine na kowa da kowa bawai zallan 'yammata ba har da iyaye." ido Feeryal ta ware ta ce "Wai da ma da daddre ne bikin ma?." "E mana kin ga yanzu za'ayi magariba ki tashi ki fara shiri, wannan kayan zaki saka." ta aje mata wani dogon rigan dokakkiyar les, had'e da gyale da takalmin da zasu hau da kayan. Miemie bata tafi ba sai da ta ga ta shige wanka. Tana fita ta gabatar da sallar magariba da aka rigada aka kira. kana ta zauna zaman shafa mai. Aunty ta turo kofa ta shigo, ta karaso cikin d'akin tana fad'in "Har yanzu baki gama shirin ba." fuska ta marairai ce ta ce "Nayi wanka fa Ammie kaya zan sa." Aunty ta d'aga kayan da Miemie ta ciro mata dasu aje a bakin gado ta dube ta ta ce "Ya banga bra a cikin kayan ba." "Ammieee jiya fa nasa." "Dan jiya ansa sai yau kuma baza a sa ba, oh ni naga ikon Allah, laifin Maryam ce." wayarta ta d'aga ta lalub'o lambar Maryam tana d'agawa ta ce "Ya miki kyau Maryam da kika kasa gwada mata aibun rashin sa bra." "Ayya Aunty Faty wai kullum sai an d'aura laifin a kaina, kullum fa laifi na kike gani." "Ai bazan fasa ganin laifin ki ba har sai randa ta koyi sawa da kanta batare da an ce tasa ba." Aunty ta kashe wayar tana cewa "Kullum bra ya kasan ce a jikin ki kwanciya ce kawai zaki cire sa." baki ta turo tana marairaice fuska cike da shagwab'a. Aunty ta ciro mata underwear da pant da bra. ta ce "Taso maza ki saka." tana tsaye ta saka ta tayata ta karasa shirin. da kanta tayi mata d'aurin d'an kwalli, Feeryal na zaune gaban mirror Aunty tad'au sarkar da 'yan kunne na gold ta saka mata, man lips kad'ai ta saka ko pauda babu a fuskarta. amma kyawunta ya dad'a bayyana a gareta ya d'are wacce akayi awa 3 ana mata makeup. Aunty ta tsaya tana kare mata kallo sai fad'in "Tabarakallah masha'allah." ta ke. ta mika mata gyale ta yafa, ta gyara mata zaman gyalen, kana ta miko mata takalmin da Miemie ta d'auko mata, baya da tudu sosai ta zura a kyawawan fararen kafafunta. ta fesa mata turare masu sanyin kamshi. Aunty ta dubeta cike da farinciki ta ce "Miqe na ganki d'iyar albarka." ta miqe tsaye tana dariya. Aunty tayi mata hoto da wayarta tana ta yaba kyawun ta. Miemie ta shigo da sauri tana fad'in "Allah dai yasa kin gama Feeryal." ido Miemie ta waro ta ja ta tsaya tana kare mata kallo baki bud'e. ta ce "Kin ganki kuwa kamar ke ce amaryar." Feeryal ta saki sassanyar murmurshi. Miemie ta janyo hannunta ta ce "Taho mu tafi mu ake jira. "Miemie kada ku wuce karfe 10, ko ba'a tashiba ku dawo gida, kuma ku kula sosai dan Allah kada ku biyewa samaruka marasa d'a'an nan, wai tukun na ma da gaske Daddy shi ya ce kuje." cewar Aunty tana tsare Miemie da ido. Miemie ta ce "Allah Aunty shi ya ce muje tun da safe muka tambaye shi, ai ya ce ma zai je gurin d'aurin auren d'azu bayan sallar azahar wai Abba'n Feenat ya gayyace sa." Aunty ta jijjiga kai dan tasan Alhaji Sa'id mahaifin Safeenat, da suke kira da Feenat suna d'an huld'a da Daddy. ta ce "To shike nan sai kun dawo ku kula sosai dan Allah a fita kuma da addu'a." suka ce to. Suna fita suka hangi su Ameerah a jikin mota, da wasu kawayen su biyo. Sahla ta tab'a Ameerah ta ce "Kalli can ki ga wacce Miemie ta d'au ko." Nabila ta ce "Kan uba wa zata bi, lallai ma Miemie nan shine har da wani gayyato ta." Ameerah ko tun kafin su karasu take aika musu harara. kawayen nasu kuwa baki suka bud'e suna kallon Feeryal tare da fad'in "Wow." Ameerah ta dad'a b'ata rai har suka karaso in da suke. ta ja dogon tsaki ta harari Feeryal sama da kasa sannan ta ce "Ke Miemie wai ya za'ayi ki d'auko wannan kice zata bimu." "Ina ruwan ki akan ki zata tafi." cewar Miemie tana yi mata kallon sama da kasa. Ameerah ta wani dalla musu harara ta ce "To wlh ba a motar mu ba, ki dai san motar da zaki sata." Nabila ta ce "Gaya mata dai dan wannan motar ubanmu ne ya siya ba uban wata ba." Miemie ta ce "Ina dai babu wacce ta siyi motar a cikin ku, to ai alhamdulillahi sai ku bari sai ko wacce acikin ku ta siya da kud'in ta kafin tayi gadara da shi, na rantse dan dai kawai motar nan bazata d'auke mu bane dukan mu da wlh in mutuwa zakuyi sai ta shiga, mttss zo muje Feeryal direban Ammah ya kaimu, daga nan ku had'iye motar a cikin ku, in kuma ba haka ba to wlh duk randa fita ta kama mu sai ta shiga, in zaku mutu sai dai ku mutu." taja Feeryal sukayi sashin Ammah. Ameerah ta ce da kawayen nasu "Dalla kuzo mu tafi muna b'ata lokacin mu anan." Hafsat d'aya daga cikin kawayen nasu ta ce "Haba da kun bari ta shiga nan ai, ni wlh tagama tafiya da ni kamar na kwana ina kallon ta, sai kace ba 'yar'uwar ku ba kuke hantarar ta haka." Ameerah ta yamutsa fuska ta ce "Wa wannan aljanar babu abin da ya had'a mu da ita, 'yar tsintuwa ce ba dangin mu ba." "Ko ni ma tayi min kyau bari mu isa muyi musanyar number na sata a friend list d'ina, wannan ka shiga da ita cikin kawaye ai girmanka sai ya karu." cewar d'aya kawar tasu Laila. bakin ciki kamar ya kashe Ameerah anyi abin da ta tsana wato yabon wata bayan ita, sai taji ta dad'a tsanar Feeryal. har suka isa tana jan tsaki da yin kwafa. Motar su ta riga nasu Miemie isowa. Feenat ta tare su da murna tana mu su oyoyo, ta jasu ta kai su gurin zaman da ta tanadarmu su. ta cike su da kayan motsa baki Zaman su da kamar 20min motar su Miemie ya iso. suna shigowa Hall d'in kallo ya dawo kansu. Feenat ta mike da gudu tazo ta rungume su, Feenat dama ita tasan Feeryal sau biyu suna had'uwa da ita idan tazo gurin su Miemie. ta ce "Kai Feeryal gaskiya naji dad'i ganin ki taho muje ku gaisa da su Mommy da ango da amarya. taja hannun Feeryal Miemie ta biyo su tana cewa "Au ita kad'ai ma kakaji dad'in zuwan ta to mu bari mu koma." sukayi dariya. dai dai sanda suka karaso zasu ratsa ta tsakiyar filin. MC ya canza wata zazzafar waka, bai sai kaji gurin ya amsa da hele ba. ya yin da camara ya saito su yana ta kashe musu hotuna masu d'aukar video suma suna yi. Feeryal kunya kamar ta nitse kasa, Miemie da Feenat kuwa sai wani fankama sukeyi. suka janyota cikin takama, ita ko da kyar take iya d'aga kafarta har suka iso gurin zaman ango da amarya. Feenat cikin rawar kafa ta ke fad'in "Feeryal Miemie ga ango Ya Mujahid ga amaryar tamu Aunty Nuwaira, Ya Mujahid kawaye na ne wannan Feeryal wannan Miemie." ta nuna ko wannen su. Mujahid ya fad'ad'a murmushin sa ya ce "Mun gode da ziyartar taya mu murna." "Bayan naku sai namu da ita wlh ni naga mata." maganar abokin ango ke nan Ibrahim daya taso daga gurin zaman sa. yana d'aya daga cikin mazajen da suka kasa control d'in kansu da ganin ta har sai da ya iso gare ta. Mujahid ya yi dariya ya ce "Allah aboki na." "Insha'allahu kuwa akwai Mom d'ina anan bari na kirata tazo shaida ga surukarta nan." Feeryal dai kasa tayi da kanta. suna kokarin barin gurin suka jiyo magana a bayan su. "Ina surukar tawa take, wacece haka ta birkita min lissafin my son?." Feeryal takuma yin kasa da kai. Mom in Ibrahim ta leko fuskarta tana fad'in "Ah lallai ba shakka dole ka rud'e insha'allahu kuwa ka samo mata, Feenat kawarki ce ko daga ina ta taho?." kai Feenat ta gyad'a tana murmushi, ta ce "Daga gidan Alhaji Abubakar Fiya." "Masha'allah zamu dangana da gidan kuwa domin a bamu ita." Ibrahim ya kankame hannun Mom d'in sa ya ce "Mom dan Allah yau aje." ta dunguri goshin sa ta ce "Ba yau ba kam sai gobe." Feeryal kam takasa cewa komai kanta na kasa tana wasa da 'yan yatsunta su Miemie nata dariya. Feenat ta ja su zuwa gurin su Mommyn ta tagabatar da su, a gurin Mommy'n ta da kawayen ta. atake a gurin wata hajiya ta ce tayi wa d'anta kamun Feeryal. Daga can in da su Ameerah ke zaune suna kallon duk abin da ke faruwa, sun cika sunyi tab kar Ameerah taji labari. har sai da ta gaza b'oye kishin ta ta ce "Lallai ma Feenat mu da muka zo kan lokaci ma bata gabatar da mu ga kowa ba, sai masu zuwan kurarren lokaci su ake wani gabatar da su kamar wasu kwamishinoni, mttsss aikin banza, ni yanzu ma zan tafi." A d'an gefe da su Ameerah Feenat ta sama wa su Miemie gurin zama. suna zama wasu maza guda biyu suka dumfaro in da suke. cikin kasa da murya Miemie ta ce "Feeryal ga wasu gayu fa suna zuwa nan, kalli can yadda wasu gungun gayun ma ke kallonki, gaskiya ke me sa'a ce, dalla ki ware jiki kiyi abu kamar wayayyiya, sai wani shan jiki kike." "Miemie nikam mu tafi." tafad'a tana sunkuyar dan tana d'agowa taga idon mutane a kanta. "Sannunku 'yammata ko zaki samin number ki?." d'aya daga cikin samarukan da suka iso gurin su ya fad'a yana mikawa Feeryal wayarsa. Feeryal tayi shiru batayi magana ba. Miemie ce ta karb'a ta saka masa lambar ta mika masa. ya amsa tare da fad'in "Thanks." kana suka koma gurin zaman su. Feenat ta kawo musu drinks da d'an abin motsa baki. Miemie ce ta ci Feeryal kam ko drink bata iya sha ba, dan gaba d'aya a takure take idon jama'a ya takura mata. anata gudanar da shagalin biki. MC ya gayyato kannen ango zuwa fili. Feenat ta ja su Miemie, Feeryal ta make kafad'a tace suje ita kam bazata iya ba. duk yadda Miemie tayi ta tashi fir taki. haka suka kyaleta suka je gurin su Ameerah. Feenat ta ce "Ameerah Sahla Nabila Hafsat Lailat ku zo mu shiga fili ga MC na kiran mu." duk suka mike ban da Ameerah da ta b'ata rai. "Ameerah ta so mana." cewar Feenat. ta ce "Kuje kawai bazan shiga ba." bata kuma mata magana ba jin MC na ta nanata kannen ango su fito, suka garzaya cikin fili aka sakar musu kid'a suka sunkuya tika rawa. Feeryal sai murmushi take sakewa idanunta akan su Miemie da suke ta cashewa. bata yi aune ba taji saukar lips d'in mutum kan kumatun ta. dai-dai lokacin kuma hasken camara ya haske su. a razane ta juyo wanda jin hakan ya bada dama wajen dai-dai tar fuskarta da tashi, nan ma hasken camara takuma haska su. a razane ta mike tsaye tana binsa da kallon tsoro. shigo gayan murmushi ya mata tare da kashe mata ido ya ce "Hi baby haupa." yaja kujerar ya zauna yana fad'in "Zauna mana muyi hira, nifa sonki nake ko zamuje mu sha ice cream." da sauri tayi baya dan ba karamin tsorata da shi tayi ba. Ameerah ta mike tsaye tare da jefa wayar ta cikin jaka, da sauri ta shige cikin filin ta ja hannunsu Sahla da Nabila, suka fito. suka ce yaya dai Ameerah?. ta ce "Ku taho mu tafi gida yanzu fa karfe goma da rabi, kafin mu isa 11 ta wuce." tayi gaba suka biyo ta a baya suka shige mota dama direba na zaune a ciki yana jiran su sukayi gida. Feeryal na tsaye jikin ta na b'ari shiko yana zaune idanunsa a kanta yana latsar lips d'in sa da kanne mata ido. "Gashi kamar wayayyiya kina abu kamar na marasa waye wa, muje hotel ki tayani kwana duk abin da kike so zanyi miki, zan kuma sallame ki da 2 million, idan baki aminta da ni ba zan iya using da condoms." Jikin ta ya d'au b'ari tsoro yadad'a bayyana a gare ta. maganar Miemie taji a bayan ta "Feeryal wai rawan ne baki iya ba ko me." da sauri ta waigo murya na rawa ta ce "Miemie mu tafi gida." mikewa ya yi yazaro kati cikin aljuhun sa ya aje sa kan table d'in gaban su ya ce "Idan kin yanke kuhunci zaki iya nemana ta wannan katina ne, I'm waiting for you, kiyi shawari da kawar taki ina jiran ki ko yaushe." ya juya ya bar gurin. Miemie ta bi bayansa da kallo tana fad'in "Wai mene ne Feeryal?." Feeryal tayi rau-rau da ido sai ga hawaye sharr, ta d'aura yatsar ta kan kumatun ta sannan ta ce "Kiss yamin a nan sannan ya ce wai na bishi hotel." ido Miemie ta waro ta ce "Shine baki masa kaca-kaca ba kika tsaya kina masa kallon tsoro, d'an iska ina yashiga na tara masa jama'a anan awa d'an iska dukan tsiya." "Miemie ki rabu da shi ni kam mu tafi gida kawai." tayi maganar hawaye na ci gaba da zuba a idon ta. "Dan Allah share hawayen ki kar kisa mutane su tsaya kallon mu, na gane shi ai wlh sai na nemo shi, tsaya Feenat ta zo tace mu jira ta." Feeryal ta share hawayen ta da tafin hannunta. Miemie sai masifa take tana d'urawa mutumin zagi. sun b'ata lokaci a zaune kafin Feenat ta dawo gurin su. lokacin karfe 11 saura minti 15. suna fita Ibrahim ya biyo su, nan suka kuma b'ata lokaci har 11 ta cika, kafin suka d'auko hanyar gida. Su Ameerah kuwa karfe 10 da mintuna 50 dai-dai suka ido gida. direba na gyara parking a babban parking lot suka fito. suna tafe kowa zai wuce sashin su suka hangi Abdurrahim zaune cikin wani kayataccen zagayayyen gurin da aka zagaye shi da fulawowu masu kyau da kawa, sama d'an rumfar bukka ce mai zawaye da koyayen wuta, kasan rumfar kujeru ne. gurin haske ne sosai kamar tsakiyar rana ba dare ba. yana zaune laptop na gaban sa yana danne-danne a cikin sa. "Kuzo nan." yafad'a idanunsa akan laptop. kallon junan su sukayi, kana suka janyo kafafunsu inda yake. suka durkusa a gaban sa. sunkai minti 5 bai ce da su komai ba kuma bai d'ago ya dube su ba, yana ta aikin latsa laptop d'in sa. Zuwa can ya soma magana "Ina kuka fito har 11 na dare kuna waje?." Suka had'a baki wajen fad'in "Munje dinner yayan kawar mu ce." sai a lokacin ya tsai da abin da yake ya d'ago ya dube su d'aya bayan d'aya sannan ya ce "Da daddaren nan sabo da rashin mafad'i ko me, ina Miemie ta ke?." da sauri Ameerah ta ce "Samarukansu ne suka d'auke su bamusan ina suka je ba." "What! samarukansu ita da wa?." ya furta yana duban su, abin ya bala'in bashi mamaki wai wad'an nan 'yan hanci wai su ke da samaruka. ta ce "Ita da Feeryal kuma da ganin su 'yan iska ne, samarukan, sai da na ce su zo muje gida suka ki." tana rufa baki motar su Miemie yana shigowa gidan. duk suka bi motar da ido, su Nabila kirjinsu na dukan uku-uku Ameerah tayi karya ta janyo musu. ya yi shiru idanunsa akan laptop yana tuka maganar cikin ransa. Kasancewar motar Ammah ce direban ya yi kokarin wucewa sashin ta da su. da sauri Miemie data hango su Sahla durkushe a gaban yayan nasu ta ce "Tsaya-tsaya mu sauka anan sai ka wuce, Feeryal sauko muje ga su Ameerah can gurin Ya Abdurrahim." suka sauko jiki a sanyaye kar Feeryal uwar 'yan tsoro taji labari. a hankali suka karaso suka sunkuya kamar yadda su Ameerah sukayi. a fusace ya d'ago ya ce "Miemie har kinyi girman da zakibi samari a mota!." ido ta waro murya na rawa ta ce "Wlh Ya Abdurrahim babu wanda muka bi direban Ammah ne ya kaimu kuma shi ya dawo da mu." da sauri Ameerah ta ce "Bayan muna ganin ku da su har wani ya yi wa Feeryal kiss, daga nan kuma kuka bisu kuka tafi." da sauri ya kuma d'ago kansa karaf suka had'a ido da Feeryal da tsoro ke kukarin tafiya da numfashin ta. maganar Ameerah ce ya sashi mai da dubansa gareta "Na rantse ya mata kiss a gaban jama'a ma kuwa, ai gasu nan." ta mika masa wayar ta, hoton Feeryal karara wani yana mata kiss, ga d'ayan fuskarsu daf da juna har suna gogar fuskar juna. Miemie ta marairaice murya ta ce "Kai Ameerah kiji tsoron Allah a'ina akayi hakan." a fusace yad'a go wayar ya nuno musu fuskar wayar. Feeryal tayi wani irin zabura, jiki na kyarma.........! Mommyn Twins ce Wani irin sarawa kanta ya yi da sai da ta kai hannu ta dafe kan, tana girgiza kan cike da matukar tsoro. hanjin cikin Miemie ya kad'a. cikin fusatacciyar murya ya nuna Feeryal da hanu ya ce "Ke tashi kibar nan!." ya fad'a cikin tsawar da sai da ta zabura ta zube kasa kana ta mike da gudu ta yi hanyar sashin Aunty. b'acin rai karara ake hangowa kan fuskarsa, ya mike a zafafe tare da d'aukar belt dake ajiye a gefensa. yashiga nad'e shi a hannunsa yana fad'in "Wato kun zama 'yan'iska kamar ku d'in nan har kun iya biyewa sa maruka, yaushe ne aka haifeku!." Ameerah ya damko yana cewa "Wato ke har kin iya d'aukar hoto ana bad'a la, ga kinan 'yar iska ko." yashiga shinfid'a mata belt tana ihu sai da ya mata taya-taya kafin ya sake ta, ya bita da naushi, tana tsalle tana sosa in da aka zuzzuba mata bulala. su Sahla kam tuni suka fashe da kuka tun kafin a zo kansu. ya cafko Nabila itama ya birkita ta da duka, yana sakin ta ta zube kasa tana kuka. haka Sahla ma. Miemie ce dukan karshe yadda taga yake huci yana dad'a kyara rukon betl d'in tasan yau kam zataci uban ta, ai kuwa dukanta yafi na kowa, sai da ya mata bulala ashirin da biyar kafin ya kyaleta. sannan ya nuna su ya ce "Daga yau wata ta sake sa kafa ta fita a gidan nan ta gani, ku tashi ku bani guri a nan!." da gudu ko wannen su ya yi hanyar sashinsu. Ganin yadda Feeryal tashigo a firgice Aunty da tun d'azu hankalinta yake tashe ganin karfe goma yayi basu dawoba. har 11 tarinka kiran wayar Feeryal d'in saijin ringing d'in sa a d'akinta tayi. wayar Miemie kuwa yana shiga ba'a dagawa. tajawota dasauri tana dad'in "Ke Feeryal lafiya meyasa baku dawo akan lokaci ba sai yanzu, meyasa kuka zauna meyafaru naganki Hak?." Aunty tana maganan cikin tashin hankali. Feeryal ta kankameta tana kuka bata b'oyemata komai ba tafad'a mata duk abin da ya faru. Aunty taja Numfashi cike da fargaba tace "Yanzu ina su Miemien suke, suna gurin yayansu kenan?." Feeryal tace Eh. Aunty tatsaya shiru kana taja hannunta suka shiga d'aki. Tana fad'in "Shiyasa tunfarko banso tafiyan nan nakuba, samari 'yan bana d'ayan nan basu da tabbas, shiyasa kullum magana ta baiwuce ki kula ba, Feeryal Allah ya yi miki baiwar zubin halittar da ba kasake za'a barki ki rika yawo ba, fitar nan sam bana son shi sai ya zama dole." Aunty ta rika fad'a Feeryal da har lokacin tsoro bai gama sake ta ba, sai sharar kwalla take. sai kuma Aunty ta shiga rarrashin ta, kana ta taimaka mata ta cire kayan jikinta ta shiga bandaki tayi wanka tafito. tagabarta da sallahn isha tasa kayan bacci ta haye gado takwanta, tare da sunkulewa guri guda tana rarraba ido cikin tsoro. har lokacin Aunty nacikin d'a kin tasata tayi addu'ar bacci kafinnan tafita . Takai zamani guda batayi bacci ba tana sake-sake a ranta sai chan bacci barawo ya sami damar yin awon gaba da ita. Nabila ta shige sashin su a guje tana mussuke jikin ta inda ta sha bulalu. Umma Karima ta zabura da sauri tana fad'in "Ke lafiya yaya haka?." Nabila ta zube gefen ta tana cewa "Ya Abdurrahim ne ya bige mu." "Duka kuma a laifin me?." Umma Karima tayi tambayar tana yamutsa fuska. Nabila ta gyara zama ta shiga fesa mata labarin abin da ya faru karya da gaskiya. Umma Karima ta ware ido tare da buga kirji ta ce "Ita da laifi ku da duka! jar'uba har ta iya tsotsar bakin namiji a cikin bainin nasi, baiyi kasa-kasa da ita ya farfasawa shegiya baki, muga bakin da zata tsotsi bakin wani namijin da shi ba, ai wannan yarinyar tajima tana iskanci tun tana kankanuwar, tafiyarta Abujan da taje ma iskanci take acan ai munsan komai, gashinan asirinta na kan tonuwa kad'an ma ke nan, in Allah ya yarda asirinta yarika tonuwa ke nan, sai tabar gidan nan, ai abin da yasa Abdurrahim ya koreta ba zai iya yiwa kazanta hukunci ba, ai sai dai ku tsaftatattun kannen sa, ta ya zaiyi yayiwa 'yar'iska hukunci, hukuncin ta ke nan kora gidan ma gaba d'aya zata bari, yanzu kam alkadarin ki Fatima ya karye daga zaran Abdurrahim ya ce ta bar gidan nan dole zata bari, hahahaha." ta karasa maganar da shekewa da dariya tana tafa cinya. Washegari kuwa Umma karima har da kiran Ameerah ta zo ta nuna mata hoton. Umma Karima ta rike baki ta ware ido kan wayar tana fad'in "Tabd'i jam lallai yarinyar nan cikakkiyar 'yar'iska ce asirinta yarika tonuwa ke nan." Sai da rana kafin Miemie tashigo sashin su Feeryal. a falo ta tadda Aunty da Feeryal d'in zaune, ta zauna tare da gaida Aunty, ta amsa tana cewa "Kunyi rashin hankali Miemie da kukakai goma awajen taron nan, watakilama shiyasa maza suka bibiyeku, da kundawo kan lokaci da duk hakan bai faruba, Allah dai yatsare yasa yayanku baimuku komai ba dai?." Miemie taja rigarta tagwada wa Aunty shatin bulala Aunty tawaro ido tace "Subhanallah abin da ake guje muku ke nan Miemie yanzu ina amfanin sa, sam fitar dare ba na d'iya mace bace, Allah shikyauta gaskiya ku rika kiyayewa." Feeryal kaman zatayi kuka ganin shatin bulala a jikin Miemie. ta ce "Wayyo sannu Miemie dan Allah kiyi hakuri ." Miemie tayi kwafa ta ce "Wallahi bazan kyale Ameerah ba, ba ita ta iya munafurciba dukda tare aka bige mu." Aunty ta ce "Kiyi hakuri kar kice zakuyi fad'a da ita tunda itama anbigeta, ki rabu da ita kawai, ku dai kurika kiyaye abin da zai janyo muku laifi." Miemie sai kwafa take tana cize lips. Aunty tayi kitchen tana saka lamarin aranta sam bataji dad'i ba da Abdurrahim bai hadasu da Feeryal ya musu hukunci dukan su ba, tun da in laifin ne tare sukayi, ya ware kannensa kenan yamusu hukunci?. ta girgiza kai kawai tana shigewa kitchen. "Ke Ameerah kada kiyi gigin cewa zaki yad'a hoton nan a Media dan wlh idan kika kuskura Ya Abdurrahim ya ci karo da shi sunan ki sorry, sai ya yi miki kabarin da ba sallah, jiya ma ke nan ya yi miki dukan d'aukar hoton bare kuma kin yad'a shi wa duniya, zai ce dama kin saba yad'a hotunan batsa wlh mukam babu ruwan mu." cewar Sahla da suke tare da su Ameerah a parlour'n Mommy. Nabila ta ce "Gaskiya nima dai ban bada goyon baya ba, kibari Ameerah mu aje hoton nan zai zame mana makami nan gaba, ai shegiya banso Ya Abdurrahim ya barta ta ba, da ya mata shegin duka 'yar iska yanzu kam mun gama da ita babu wanda zai zo gurin ta, in yazo kuwa sai ya gani." Sumayya ta rike hab'a ta ce "Hm wlh Ameerah kibi ahankali ku rabu lafiya da Ya Abdurrahim, ina dukan da ya miki akan d'aukar hoton ne shine zaki ce zaki yad'ashi wa duniya, idan fa kika kuma shiga hannunsa bazaki ga da kyau ba." Ameerah ta ja tsaki "Mttss ai na rantse da Allah yadda aka bige ni sai an bige ta, wulakantaccen duka ma kuwa, da wayarta zanyi sending hoton wa duniya kowa ma yagani ta yadda kowa zai d'auka ita d'in ce ke tallen kanta wa duniya." Sumayya ta gorgiza kai ta ce "Ameerah nadai gaya miki kibi a sannu, idan ta kwab'e miki bazakiga da kyau ba." Ameerah ta mike tana hararar Sumayya ta wuce d'aki, cike da shan alwashin sai ta aikata. Bayan kwana uku da faruwar haka da sauri Miemie ta shigo sashin Auny. A parlour ta tadda Feeryal ita kad'ai tana zaune tana kallo a TV. Miemie ta zauna kusa da ita tabuge cinyar ta tana fad'in "ke Ibrahim yakirani fa tund'azu, ya d'agamin hankali shiyasa ma nazo amma tun d'azu ina kwance ne banyi niyyar zuwa gurin ki ba, tun da ke tsoro ya hanaki fitowa kizo in da nake, matsoraciya kawai, sai aka ce miki kuma shi Ya Abdurrahim d'in duka yake haka kawai babu dalili, kuma ma ai dukan da ya min ni nasan har da naki ya had'a dan duka na yafi na kowa tun da tare muke da ke, tare Ameerah ta kulla mana sharri." Feeryal ta marairaice fuska batayi magana ba sai narai-narai da ido take suna kokarin kawo kwalla. Miemie ta ce "Bari na kirashi dan ya ce yayi ta kiran ki baki d'aga wayan sa, nace kad'an daga aikin ki." tana kokarin kiranshi Feeryal ta ce "Ni dai Miemie da kin barshi to mezanmishi." Miemie ta ce "Ke dallah wannan had'add'an gayen, kuma yace zai zo na ce wallahi yazo." Feeryal taware ido ta ce "Wallahi babu ruwana Miemie yazo ina baburuwana." Miemie ta ce "Ke wlh dad'ina dake tsoro, da har dake aka buga ranar da ban san ya zakiyi ba nasan har fitsari sai kinyi tsabar tsoro, ke wallahi Ibrahim dagaske yakeyi ya ce aure yake son yi babu wani bata lokaci, ya ce yana zuwa yau gobe babansa zaizo." kafin Feeryal tabata amsa Aunty tafito. Miemie ta ce "Yauwa Aunty dama wanine sunansa Ibrahim muka had'u da shi agun bikinan ya ce yana son Feeryal, abokin yayan Feenat ne ya ce zaizo yau gobe kuma yaturo magabatansa anemamasa izini gurin daddy." Aunty taware ido ta ce "Badai shine kuka hadu da shi ya yi mata rashin d'a'ar nan ba?." Miemie ta ce "A'a wlh Aunty bashi bane wannan mutumin kirkine kuma yana sonta, abokin yayan Feenat ne ma har Mom d'in sa ya nuna mata Feeryal." Aunty tad'anyi shiru sannan ta ce "Amma dai yafara neman Daddy'n tukunna, in ya amince sai ya zo." Miemie ta ce "Ya ce zai turo babansa gobe yau zaizone kawai ya tambaye ta da kansa idan ta ce ya tura sai ya tura." Aunty tace Allah yakaimu. Dayamma wajen karfe 4:40 saiga kiran Ibrahim awayan miemie yazo yana bakin gate. Miemie tazo tasa security suka bud'e masa gate takaishi bakin sashin Aunty. ita tashiga ta kirawo Feeryal, dakyar Feeryal tafita sai da Aunty ta ce mata taje tadawo karta dad'e. tafito da babban hijabi tunkafin takaraso inda yake, ya kafe ta da ido yana fadin "Masha'allah wallahi kamar da hijab d'inma kinfi kyau." Feeryal takaraso a hankali ta d'an tsaya gefe da shi ta ce masa "Inayini." wani murmushi ya sake idanunsa a kanta. Miemie ta ce bari tad'an basu guri tayi falon Aunty tazauna. Feeryal natsaye Ibrahim nata zayyane mata kalan son da yake mata shifa nan da wata d'aya yakeso ya aureta. Feeryal dai batace kalaba sai hijabin dataja tarufe gefen fuskarta. yaleko fuskarta yana fadin "Bud'e mana inata magana bakice komiba, kitsaramana yadda zamu gudanar da shagalin bikinmu." jan hijabin tadayi tana murmushi tarufe fuskarta sosai. salati sukaji abayansu ana tafa hannu. "Innalillahi wa innailaihirraji'un! lallai kun shahara wato iskancin naki harcikin gida, abin naki ya girmama har maza kika fara kawo mana su cikin gida kuna sheke ayarku, iskancin naku har gida!." Umma karima tayi maganar cike da hayagaga takawo hannu tad'aura abaki tana tana fad'in "Yihuhu jama'a kuzo nakamasu, na kamasa da idona." Ibrahim yatsaya yanamata kallon mamaki, Feeryal ko gaba d'aya jikin ta ya d'au kyarma........! KUYI HAKURI DAN ALLAH BANI DA BAKIN DA ZAN IYA BAKU HAKURI WLH SAM BANSO HAKAN TA FARU BA AKASI AKE TA SAMU KWANA BIYU, DA DAREN NAN NASAMU NAYI WANNAN KUYI HAKURI DA SHI DAN ALLAH *Assalamualaikum barkanmu da wannan lokaci barkanmu da dawowa hutun Ramadan anyi sallah lafiya Allah ya maimaita mana ya karbi ibadun mu* Ibrahim ya bita da kallo ganin kiri-kiri da gaske sharri take son gina musu, ya ce "Me kike nufi ne wai? muna tsaye muna hira ki ce kin kama mu, kin kamamu muna me?." da karfi ta ce "Iskanci iskanci na kama ku da idanun nan nawa kiri-kiri ka shige cikin hijabi kana kwakularta, munafukan Allah ta'ala asirinku ya tonu. jama'a kuzo na kama 'yan'iska." kan kace me ma'aikatan da suke aiki a babban kichin sun taho gurin. Umma Karima bata fasa kwalala ba fad'i ta ke "Na kamasu wlh na gansu da ido na, ya makale cikin hijabin ta suna aikata masha'ar su. Mommy da Mom akusan tare suka iso gurin 'ya'yan su sun kaimusu rahoto. sai tafa hannu suke da sallalami. Ammah da mai aikin ta ta sanar mata da abin da ke faruwa ta fito abujajan. Ibrahim na tsaye ya cika da mamaki matuka. Mom ta rike hab'a tana sallalami, da fad'in "Ai dama akwan a tashi in dai halin mutum ne sai asirinsa ya tonu, a had'asu da karnuka da security su rakasu da duka 'yan'iska tambad'ad'd'u, zaku kawo mana iskanci har cikin gida." cewar Mom tana aika wa Ibrahim da Feeryal banzan kallo. Ammah data karaso gurin tayi saurin cewa "A'a baza'ayi haka ba zo ka wuce katafi abinka kaji bawan Allah." Mommy ta ce "Kamar ya zakice ya tafi Hajiya Safiyyah ai yazama dole su karb'i hukun ci dukkan su shi da wacce ta jajub'o sa." Ammah ta girgiza kai ta ce "Ashsha ai ni banga shaidar da ke nuni da abin da ake zargi ba, mutum d'aya bai wadatar da bada shaida kan zina ba, a cikin ku akwai wannda ta gani da idon ta bayan Hajiya Karima?." Ammah tayi tambayar tana tsaresu da ido. duk ma'aikatan suka girgiza kai, Ammah ta ce "To kaje abin ka kaji, dan kuma Hajiya Halima da Hajiya Nafisat kusan a tare muka iso nan da su, babu wanda acinin mu zai bada shaidar abin da ake zargi, dan ita zargin zina sai ana da kwararan shaidu guda uku wad'an da suka gani da ido." Ibrahim yaja kafarsa yana girgiza kai yama kasa iya cewa komai, tsabar mamakin matar, ya shige motarsa ya bar gidan baya ko ganin gabansa. Gaba d'aya gurin ya kacame da hayani Mommy da Umma Karima da Mom, sai bala'i suke suna fad'in yarinyar da kowa yasan ita 'yar'iska ce a filin Allah cikin bainin jama'a take iskanci, har ana d'aukarta hoto da video waye bai san 'yar iska bace. Aciki kuwa TV da yake a kunne ne ya hana Aunty da Miemie jin abinda yake faruwa da wuri, sai da hayaniyar ya kara yawa kafin suka jiyo hayaniyar sosai. da sauri suka nufo waje. Aunty ta tsaya cike da mamaki tana jin abinda yake faruwa cikin b'acin rai sosai ta dubi Feeryal dake tsaye ta toshe bakin ta da hijabi tana hawaye ta ce "Ke Feeryal da gaske kin aikata abin da suke fad'a?." da sauri ta girgiza kai murya na rawa hawaye na zuba ta ce "A'a Ammie." hannun Feeryal Aunty ta janyo ta dawo da ita kusa da ita sannan ta dubi Umma Karima ta ce "Hajiya Karima kin dai ji da kunnen ki ta ce bata aikata ba, to kuwa tabbas bata aikatan ba, ki tsaya a matsayin ki kada ki sake shiga lamarin ta bai shafe ki ba." "Iye lallai ma kuwa ba shakka! irin ga waliyyiyar nan wacce bata fad'an karya daga ta fad'i magana gaskiya ce, tana aikata iskanci kiri-kiri a kamata dan ta ce batayi ba shike nan ya zauna a kan bata yin ba." Aunty tayi saurin katse ta "Ni na yarda da d'iyata idan da ta aikata nasan bazata tab'a yi min karya ba zata fad'a min, dan haka bata aika ta ba, kowa ya kama gabansa kubar min kofar side!." Nan da nan ma'aikatan kowa ya kama gabansa. Umma Karima tayi shewa tare da tafa hanu tana fad'in "Ahayyeee rass. ke har kina da bakin fad'ar wannan maganar yarinyar da gata nan cikin hoto kiri-kiri tana rungume da wani katoton gardin d'an iska, a cikin bainin nasi kowa ya gani babu wanda bai sani ba, an dai ji kunya wlh, an aje katuwar 'yar'iska a gida ana son ta b'ata mana yara" Aunty ta yi saurin katse ta "Ki iya bakin ki Hajiya Karima kar ki kuskura ki wuce gona da iri, zakiyi nadamar bakaken kalaman ki." Mommy ta watsawa Aunty kallon banza tana cewa "Bafa zai yuwu ba yazama dole ayi zama da Alhaji dan wlh bazamu zauna da 'yar iska ta gurb'ata mana rayuwar 'ya'ya ba, Ameerah Sumayya wuce mujen ku bari Alhajin ya dawo." Mom ma ta kad'aga keyar Sahla bayan ta gama fad'an miyagun maganganun ta. Umma Karima ta dubi Aunty tana fad'in "Hajiya Fatima alkadarin ki na daf da karyewa, dan bazamu bar tsintacciyar agola cikin 'ya'yan gida ta koya musu iskanci ba, na fad'a na kara fad'a, kiyi abin da zakiyi." Siyama ta yamutsa fuska ganin kamar tana son yin magana Miemie ta dalla mata harara. Umma Karima ta kad'a keyar nata iyalan Bilkisu Rahma Saddiqa Nabila Siyama suna gaba tana bayan su. Ammah tabi bayan su da kallo kana ta girgiza kai tana fad'in "Agwagwa ke nan 'ya'yan ki nagaba kina baya, mugun abu yabi dare cikin duhu Allah shi kyauta, kiyi hakuri Feeryal, Hajiya Fatima sai dai ayi ta hakuri dan wad'an nan mutanen halin su sai su." Aunty ta ce "Mugun nufin su ya kare a kan su, insha'allah abin da suke son gani kuwa bazasu gani ba, haka zasu kare da kai kawo." ta ja hanun Feeryal suka shige ciki Miemie ta biyo bayan su, Ammah kuma ta koma sashinta tana mai mamakin hali irin na Umma Karima da su Mommy masu shaidan zur. Ibrahim a hargitse ya isa gida, yana dai-dai ta parking ya fita da sauri ya nufi sashin Mom d'in sa. ganin yadda ya fad'o cikin parlour da sauri ta tare shi tana fad'in "Son lafiya me ya faru mene ne!?." a binka da d'an gatan da bai saba shiga damuwa ba ya labarta mata abinda ke faruwa cikin matukar damuwa. Mom d'in sa ta waro ido ta ce "Wlh karya ne bazai yiwuba dole a wanke zargin da aka maka a gaban kotu, daga zuwa niman aure dan baza'a baka ba sai a bika da mummunar kazafi, to wlh bazan lamunta ba sai mun d'au mataki." ta d'aga waya ta kira lambar Dad d'in sa ta sanar masa abin da ke faruwa. baya kasar amma yace sabo da faruwar haka zai dawo, dan ya ce bazai lamunce wulakanci da tozarci kan d'ansa d'aya tilo ba. amma da jin ko a wani gida lamarin ya faru ya ce bazai dawo ba amma zai nimi Alhaji Abubakar d'in da kansa, dan yana ganin mutuncinsa dan yasan shi mutum ne mai mutunci. nan da nan ya nimi Daddy a waya, Daddy yana hanyar dawowa gida daga office kiran Dad d'in Ibrahim ya shigo wayarsa. Umma Karima najin shigowar Daddy, ta nufi sashin Mommy da sauri, tana shiga ta isketa a parlour tun kafin ta karaso take fad'in "Hajiya Halima taso maza muje naji shigowar Alhaji kafin wancan makiran matar can tasa, ta rigamu zuwa ta je ta kitsa masa makirci yahau ya zauna a kai, gara a yi ta ta kare yau 'yar nan ta bar gidan nan, badun Hajiya bata gari ba, ai da anyi ruwa an d'auke." "Ai kuwa maza muje dan ni tun da nake ban tab'a ganin makirarriya irin Hajiya Fatima ba, tagama da Alhaji gaba d'aya wlh ji nake kamar ta mutu na huta." "Hm kyale munafukar can taurin rai gare ta amma ajuri zuwa rafi saura kiris tulu ya tarwatse." cewar Umma Karima tana jinjina kai. suka fita suka nufi sashin Daddy. Daddy na zaune a parlour'n sa dan da ya shigo a parlour ya zauna bai shige ciki ba. har suka shigo suka sami guri suka sauna bai d'ago ba yana abinda yake yi. suka had'a baki sukayi masa sannu da dawo wa, ya amsa, batare da ya d'ago ba. Umma Karima ta d'an tab'a Mommy tayi mata alamar ta fara magana. Mommy ta gyara zama tare da fad'in "Alhaji mun zo gurin ka ne, yanzu fisabilillahi Kai kaji ka amince 'ya'yan ka su zamo tambad'ad'd'u ta sanadiyyar 'yar da ba'a san asalinta ba ma, bafa zai yuwu ba yazama dole a kawo karshen lamarin, iskancin yarinyar nan ya tashi a waje ya dawo har cikin gida kana sane kayi shiru, bari Hajiya ta dawo dan wlh mu bazamu zuba ido muna gani tarika shigo mana da 'yan'iska cikin gida, ga 'ya'yan mu mata suna cikin gidan ba." Umma Karima ta ce "Ato gaya masa dai, yarinya tasan ta rika kawo 'yan'iska cikin gida suna iskanci ai abin nata ya girmama ya kai makura, da idanuna na gansu a tsaye a bakin get d'in sashin Hajiya Fatima, ya shige cikin hijabinta suna shagalin su, ni tun da nake ban tab'a ganin tambad'ad'd'iya irin aljanar yarinyar can ba." Daddy ya d'ago yana dubansu rai b'ace, ya nuna Umma Karima tare da fad'in "Sai da nayi sammanin daga gurin ki maganar nan zai fito, da Alhaji Shitu Abdu ya sanar min, ke Hajiya Karima ki kiyaye ni wai me ke damun ki ne kam Hajiya Karima? kin san waye Alhaji Shitu Abdu kuwa? to bari kiji taken sa mai kud'in shari'a, ba'a tab'a takasa a share lafiya sai ya yi shari'a da koma waye, me ya kaiki shiga lamarin sa ina ruwanki; badun yana ganin mutuncina ba da yanzu kinji sammaci daga kotu, idan kiyi wa Fad'imatu kin share, ko ince ni tunda Feeryal a gurina take nine ubanta, to Alhaji Shitu Abdu bazai jure tozarta masa d'a ba, ki dawo hankalin ki nagaya miki ke nan!." Daddy ya mike rai b'ace ya kwashi wayoyin sa ya nufi bedroom yana cigaba da fad'a. Umma Karima ta d'a murya ta nad'e taburman kunyarta da bori "Eh da ma ai zaka ce haka tun da ni mai jinin kule ne, yazo ya yi sammaci na mana muzuba mugani da ni da shi wazai fad'i a shari'ar, in shi mai kud'in shari'a ne ni mai bakin kare kai ne, haka kawai ga gaskiya muraran a nimi rufa gaskiya da bayan hanu." ta mike fuu ta bar parlour'n. ta bar Mommy nan zaune dan dama ita ce da Daddy. Koda Umma Karima ta fito zata koma sashin ta can ta hango, motar Abdurrahim da shigowar sa ke nan yana kokarin gyara parking a babban parking lot. ta karaso, dai-dai sanda ya fito daga motar ya maida marfin motar ya rufe, waya na rike a hannunsa yana kokarin tura kira. ta ce "Sannu da dawowa Abdurrahim ya aikin dai." "Alhamdulillah." ya fad'a a takai ce yana kokarin barin gurin. Umma Karima tayi saurin fad'in "Da ma yanzu nake shirin kiranka idan na koma ciki, na ce da kai idan ka dawo kazo ina niman ka." bai yi magana ba sai kiran da ya katse yana son jin abin da ke tafe da ita. ganin hakan ya sata fad'in "Abdurrahim ace kana cikin gidan nan, abubuwa da yawa suna ta faruwa a matsayin ka na babba a gida, kana ji baka d'au wani mataki ba, a kaf gidan nan fa daga alhaji sai kai, ko kannensa Alhaji Sulaiman da alhaji Tukur sai dai su biyo bayan ka su jira umurnin ka, dan kaine Alhaji karami. amma ace sanannen gida kamar wannan a aje tukururuwar karuwa aciki tana d'ebo 'yan'iska tana shigo wa da su har cikin gidan nan, ba'a taka mata burki ba; ai ko dan gudun gurb'acewar kannen ka zakayi wani abu, kafin ta kai ga lalata musu rayuwarsu suma, wannan yarinyar da Hajiya Fatima ta tsinto annoba ce a gidan nan, sam ba yar arziki bace irin tambad'ad'd'un aljanun nan ne, haka shekaran jiyan can ta ja su Ameerah ta kaisu gurin party, haka ta tsaya a bainin nasi tana rungume rungume da maza, ga video a wayan Ameerah kowa ya gani iskanci muraran, yau har gida abokin iskancin nata ya biyo ta, aka kamasu hanu da hanu, haba ina amfanin sa abin nata ya yi yawa." "To ni meye matsala ta da hakan Hajiya Karima? ki sanarwa Aunty'n da ta kawo ta mana, inaga zai fi." ya yi maganar yana picking na call d'in da ya shigo wayar sa, ya kai wayar kunne ya fice a parking lot d'in. Umma Karima ta bi bayansa da mugun kallo a fili ta ke fad'in "Wannan d'an iskan yaro har gobe bazai canza halinsa ba, in banda tsabar rashin daraja, ni da na zauna shekara da shekaru da uban sa da Hajiya Karima ya ke kirana, sai wancan juyar yake kira da Aunty, a sannu duk zaku dawo karkashin ikona kai da uban naka." tayi kwafa a fili, ta juya ta nufi b'angaren ta. Har ya d'au hanyar sashin sa sai kuma ya juya ya nufi b'angaren Mommy. a bakin kofar parlour ya tsaya, su Ameerah da Sumayya suna zaune cikin parlour'n ko wannen su da waya a hannunsa suna chatting. suna ganin sa kowa ya shiga taitayin sa, duk suka aje wayoyon suka shiga gaishesa. batare da ya amsa gaisuwar tasu ba ya dubi Ameerah fuska a murtuke ya ce "D'auko wayar ki ki zo nan!." da sauri ta mike ta d'au wayar ta tako gabansa kirjinta na dukan tara-tara hannun ta na rawa ta mika masa. ya amsa tare da kuma tamke fuska ya daddana zuwa can ya d'ago tare da nuna mata screen d'in wayar ya ce "Uwar me kika ajiye sa kike yi da shi a wayar baki goge ba?." da sauri tayi kasa da kanta tashiga kame-kame dan irin kallon da yake jifan ta da shi tasan babu ko shakka zata iya samin tsarabar duka. da sauri ta ce "Dama..dama.ban..bansan yana nan ba nayi zaton na goge tun ranar." wani mugun kallo ya wurga mata ta kuma shiga taitayin ta da kyau. ya mai da idanunsa kan wayar kana ya d'ago ya ce "Ina video yake?." da sauri ta d'ago ya tsare ta da ido, baki na b'ari ta ce "Babu wani video hoto ne kawai." ganin yadda ya tsare ta da ido murya na rawa ta soma rantse-rantse "Wlh Ya Abdurrahim iya hoto ne kawai na rantse da Allah babu video kuma ka duba ka gani ma." bai kuma magana ba sai idon da ya tsare ta da shi. cikin dakika guda ya karanto iya gaskiyar take gaya masa. wayar ya wurga mata kad'an ya fad'i kasa tayi saurin taro sa, ya nuna ta da yatsa tare da kad'a yatsar yana mai taune gefen lips d'in sa alamun gargad'i, kana ya juya ya fita. Sumayya da ke zaune cikin ta ya d'ura ruwa. tana ganin fitarsa ta mike da sauri ta na fad'in "Ina ga irin ta ina kinga abinda nake guje miki, hoto kawai kika d'auka a kaci ubanki da duka ina kuma ga kin yad'ashi wa media, ai wlh da baki da wata mafita gun Ya Abdurrahim zai ce dama aikin ki ke nan, yad'a hotunan bad'ala; Allah ya taimake ki." Ameerah ta dalla mata harara tana cewa "Ke nifa bana son munafurci ina ruwan ki, ai na rantse bazan kyale yarinyar nan ba sai nasa an mata dukan tsiya shegiya mai idon mayu, ai tun da aka bige ni a kan laifin ta wlh itama sai ta sha duka." "To Allah ya taimake ki Ameerah ni dai in zaki bi ta tawa da kinyi hakuri kawai." "Anki a bi takin Sumayya ke nifa bana son shishigi." Sumayya ta juya ta nufi bedroom d'in su tana fad'in "Kar ki fasa Ameerah." cikin d'aga murya Ameerah ta ce "Ai dama bazan fasa ba, na rantse sai ta duku." Sumayya bata kuma bi ta kanta ba ta shige bedroom abinta dan tasan halin ta sarai yanzu sai ta huce fushin goge hoton da yayan nasu ya yi a kanta. Hajiya bata nan taje ta'aziyya a yelwa, sai da tayi kwana uku kafin ta dawo, tun bata hutaba labari ya isar mata. ta ce wa Ajmal da ya shigo yi mata sannu da dawowa ya kira mata Daddy. shiko ya mike ya nufi kofar fita yana fad'in "Kijira ya dawo mana." "Kai Ajimi iya shege zaka kawo min, ka kira min uban ka ka ce na jira shi, gaka min iya shegen banza, ban san me Abubakar yake nufi ba, daga ce ta d'an zauna na wani lokaci kafin a gama bincike, shike nan sai ta shari gindi ta zauna har malikiyaumiddini, to bari ya dawo ya same ni zaman nata ya isa haka ta kara gaba, nagaji da gayyar tsiya arna gun idi." Da daddre Daddy da ya shigo gaishe ta ko zama baiyi ba ta taresa da maganar. ta ce gobe gobe yasata a mota ta koma inda ta fito. da kyar Daddy ya samu ya lallab'a ta ya ce saura kiris a gama binciken ana gamawa zata koma, Hajiya ta rika bala'i haka dai ya tashi ya barta β˜…β˜…β˜? Yau Feeryal tun da yamma take side d'in su Miemie, har bayan sallar isha, tun kan magriba taso komawa b'angaren su Miemie ta ki barinta. har dai da sukayi sallar isha kafin suka fito ta rako ta. suna tafe suna d'an hirar su, suka taho ta kofar b'angaren su Ajmal. Zaraddin da tun fito warsu a kan idon sa yana hango su ta saman bene, kafin su karaso ya yi saurin sauko wa. suna isowa ya fito yana wage baki. Miemie ta ce "La Ya Zaraddin ashe kana nan, kwna biyu ina ka shiga ne bana ganin ka." kirjinsa ya shafa yana bin Feeryal da wani irin mayataccen kallo ya ce "Tafiya nayi d'azu na dawo." murmushi Feeryal tayi tana janye idanunta daga kallon da ya ke mata cikin siririyar muryarta mai kama da mai yin shagwab'a ta ce "Sannu da dawowa Ya Zaraddin ka dawo lafiya." wani irin lumshe ido ya yi ya wani rungume hannunsa a kirjinsa da ke ji ina ma ace ta fad'o cikin sa, komai na yarinyar ya had'u babu makusa ko kad'an. ya karkace kai yana cigaba da aika mata irin kallon nan nasa sannan ya ce "Daku na fara had'uwa da na shigo ku yakamata ku fara kunce jaka ku kwashi tsaraba, musamman ke da kikayi min barka da dawowa lafiya." ya yi maganar idanunsa akan Feeryal. "Oh lallai ma Ya Zaraddin d'in nan amma ai ni na fara tambayar ka banganka ba kwana biyu." Miemie tayi maganar tana d'aga kiran Ammah da ya shigo wayarta. "To Ammah." ta fad'a tana sauke wayar. ta dubi Feeryal tana fad'in "Ki karasa bari naje na bawa Ammah ATM d'in ta zata aiki direba kuma ni na aje mata shi wai bata gani ba, ina zuwa yanzu." Feeryal ta gyad'a kai. Miemie ta juya da sauri. Feeryal ta d'aga kafa tana kokarin barin gurin, da sauri Zaraddin ya ce "Ah ina kuma zakije tun baki karb'i tsarabar ki ba, ai kin cancanci tsaraba mai tsoka ke da kikayi min fatan na dawo lafiya ai dole na saka miki, taho muje ki karb'i tsaraba sai kinso ki samma Miemie." ya juya ya shige kofar dide d'in su, sannan ya juyo ya ce "Zo mana zo muje ki karb'a." ya yi maganar yana gwada mata hanya. a hankali ta d'aga kafarta da zummar biyo shi. wata mota da ta shigo gidan yanzu fitilar motar ta hasko mata ido. da sauri ta kai hannunta biyu ta kare fuskata,dan har jijiyar idanunta sai da ya amsa sakamakon hasken nan. Tsawon sakanni 20 wutar motar bata janye a kanta ba. da sauri ta matsa gefe tare da janye hannayen ta kan fuskarta, sai a sannan ta sami damar iya bud'e idanunta. abin da ya bata mamaki motar tana tsaye batayi gaba ba ba'a kuma kashe wutar motar ba. maganar Miemie ta juyo a bayan ta "Feeryal muje gashi har na dawo." Miemie tayi gaba Feeryal ta biyo ta, da sauri Miemie ta d'an dawo da baya ta ruko hannun Feeryal ta ce "Motar Ya Abdurrahim ce wannan zo mubi ta can.......! *Babu editing a karanta da hakuri* Miemie ta janyo hannunta suka bi gefe. yana zaune cikin motar ya jingina bayan sa jikin sit idanunsa akan waya yana latsawa. kallo d'aya tayi masa tayi saurin janye idanunta sakamakon jin wani irin mummumar fad'uwar gaba, sau uku ke nan tun da take gidan ta tab'a ganin sa, had'uwarsu ta farko a sashin Hajiya da yake tambayar ta wai ita aljana ce ko, sai kuma ranar da sukaje dinner sukayi dare, sai kuma yau. ganin da tayi masa sau uku duk abu guda take ji mummynar fad'uwar gaba mai had'e da tsoro. duk da ba su yake kallo ba idanunsa na kan wayar hannunsa, amma gaba d'aya ta rud'e ganin irin dukan da ya yi wa su Miemie ya dad'a kara mata tsoron sa. da karfi ta damke hannun Miemie ta kara saurin ta. Suna shiga parlour Aunty ta wani sauke numfashi mai sauti. Miemie ta dube ta ta ce "Ya dai Feeryal?." kai ta girgiza tare da kakalo murmushi. A parlour suka tadda Aunty da Daddy zaune suna kallo tare da d'an tab'a hira. suka karaso suka gaishe su, Daddy ya dubi Miemie ya ce "Mamana mutumiyar taki taci abinci kuwa?." Aunty ta ce "Wani abincin cake da yogurt ba tana da abincin da ya wuce su ne." kai Feeryal ta langwab'e ta ce "Naci tuwo fa Daddy ko Miemie." Miemie tayi murmushi ta ce "Taci Daddy tare ma muka ci." "Yauwa ko ke fa gara dai a rika had'awa da mai nauyin, idan iska ya taso kinyi nauyi bazai iya kada ke ba." cewar Daddy cikin zolaya. dariya duk sukayi. Daddy ya mike ya nufi bedroom ya na cewa "To sai da safen ku." zama sukayi suka bud'e sabon hira, har wajen karfe goma kafin Miemie ta yi musu sallama ta tafi. Feeryal ma ta mike dan bacci ne cike a idanunta ta shige bedroom d'in ta. Aunty ta je ta kulle kofar parlour kana ta dawo ta kashe TV sannan ta rage wutan parlour ta shige d'aki. Ta taras da Daddy ya yi nisa a baccin sa, ta rage kayan jikinta ta sa na bacci kana ta shige bayi ta d'auri al'wala ta fito ta haye gadon itama ta kwanta gefen sa bayan tayi addu'a. wani irin zabura Daddy ya yi ya mike zaune tare da fad'in "Innailaihirraji'un!." ya dafe kirjinsa jikinsa na cirawa. a razane Aunty ta mike ta ruko shi tana fad'in "Subhanallahi ya ya dai Daddy me ya faru bakayi addu'a bane ka kwanta." kai ya girguza mata yana sauke numfarfashi tare da share gumin da ya karyo masa. gaba d'aya Aunty ta rud'e a 'yan kwanakin nan ta lura a duk sanda ya kwanta haka zai farka a birkice. tsawon shekaru ashirin da d'ori bayan auren su ya yi ta fama da irin wannan matsalar wacce damuwar haka takai ga tab'a masa lafiyar zuciya, a wancan lokacin bayan auren su da wata biyar yasoma irin wannan mummunar mafarkin, sai da ya shari shekaru goma yana fama da matsalar, da taimakon Allah da taimakon addu'o'in da Aunty take tayashi yasami sassaucin lamarin, damuwa da irin wahalar da yake sha idan ya kwanta bacci, ta kai ga tab'a masa lafiyar zuciya, da har gobe yake shan magani. sai gashiga a 'yan kwanakin nan abun ya dawo yanzu ba bu dare babu rana daga zaran ya kwanta bacci zai farka a firgice. Ganin yadda gaba d'aya hankalin Aunty ya tashi, a hankali ya kwantar da kansa jikin kafad'ar ta yana sauke numfashi. cikin shiga damuwa sosai Aunty ta ce "Daddy tashi kayi al'wala muyi sallah babu abin da yafi karfin Allah babu abin da zai faru da yardar Allah." Tarika karfafashi har ya mike yaje ya d'auro al'wala, yafito ya taras har ta shinfid'a musu sallaya ta sa hijabi tana tsaye tana jiran sa. shi ya jasu sallar suna idarwa taje ta d'auko musu Alkur'ani. sun jima sosai suna karatu cikin suratul BAQARA, sai da ta tabbatar da nusuwa tare da shi, har yana karatun yana gyangyad'i, ta gyara ta mike kafafunta ta ce "Kwanta Daddy." ya mike kan sallayar yayi pillow da kafarta. a hankali take karatun cikin kasa da murya tana yi tana shafa kansa, nan da nan bacci ya yi gaba da shi. ya yi bacci abadan kafin itama ta soma lumshe ido. ta rufe kur'anin kana ta jingina bayan da jikin gado a haka bacci ya d'auketa a zaune. Har sai kusan asuba ya farka ya ganta zaune tana bacci. kauna da tausayin ta suka dad'a shigarsa, ya mike ya ciccib'eta ya d'aurata a kan gado, yana ajeta ta bud'e ido. murmushi tayi masa cikin muryar bacci ta ce "Daddy ashe da sauran ka har yanzu tun da ka iya d'aukata." kumatun ta ya ja ya na fad'in "Tun da ina da ke kam tsufa bata isa ta matso ni ba." murmushi tayi masa ta gyara kwanciyar ta. shiko ya shige bayi ya d'auro al'wala, yafito ya haye sallaya yasoma gudanar da nafilfili. sai da aka kira sallar asuba kafin ya tashe ta shikuma ya wuce masallaci. Aunty na idar da sallah ta je ta tada Feeryal kafin ta koma tacigaba da adhkar. Feeryal ko bayan ta idar da salla da karatun alkur'ani tayi kamar yanda kullum Aunty ke umurtar ta da tayi, tana shafa addu'a ta haye gado ta koma baccin ta. ba ita ta farka ba sai wuraren karfe 11 da rabi. Bayan tayi wanka ta shirya cikin doguwar rigar atamfa da ta amshi jikin ta. ta fito ta wuce dinning ta tarar da Aunty a gun ta tanadar mata abin kaunar ta wato cake da yogurt. ta bayan kujerar Aunty ta zo ta kwantar da kanta gefen kafad'ar ta cikin siririyar muryarta ta ce "Ina kwana Ammie na." Aunty ta shafa gefen fuskarta ta ce "Lafiya lau 'yammatan Ammie antashi lafiya ya lalaci, a rage lalacin nan gobe ke zakiyi mana breakfast idan Allah ya kaimu, yau ma tare zamu shiga kitchen anjima." "To Ammie." ta fad'a tana mikewa a jikin ta taja kujera ta zauna. Kamar yadda Aunty ta ce da rana tare suka shiga kitchen da Feeryal. Sosai Aunty ta dage wajen koyawa Feeryal nau'ikan girki kala-kala, bata yadda ta barta kara zube kamar yadda wasu masu kud'in suke yi wa 'ya'yan su ba, komai sai dai masu aiki suyi ba dai 'ya'yan su ba, suna ganin wai hakan gata ne da yawa sai sunyi aure suke had'uwa da kalu bale daban-daban a gidan auren. duk da Aunty d'iyar masu kud'i ce bata taso cikin tarbiyyar irin wad'an can 'ya'yan masu kud'in ba. shiyasa ta zage damtse wajen koyawa Feeryal abubuwa da dama da suka shafi cikin gida. yawan zama da Miemie takeyi a sashin itama ta karu da wasu abubuwa da dama. Aunty ce zaune a parlour tana video call da Hajja Umma. jiya aka sami nasarar zakulo mutum biyu daga cikin tawagar 'yan d'aukar amarya, da hukuma suke ta kan bincike a kansu har yanzu. Aunty tace "Amma dai Hajja Umma babu wata matsala ko? ni fa tun da naji ance an kuma kama wasu 'yan gidan sa duk a tsoro nake, kar sauran da suke a b'oye suce zasu fito d'aukar fansa." Hajja Umma ta ce "A'a babu komai insha'allah, wannan yaro Sadam Abokin Nasir Allah dai ya saka miki, yaron akwai kokari jiyan nan kusan da shi muka wuni a gidan nan da jami'an su, da daddare ya turo jami'an su biyu da folisawa biyu da Nasir ya turo har muka waye gari yau da su, har yanzu ma suna nan, amma naji Alhaji yana cewa anan zasu cigaba da zama har zuwa a kare bincike." Aunty ta sauke numfashi tare da cewa "To Allah ya dad'a tsarewa." "Amin ya Allah, wai ni kam ina kishiya take ne banji d'uriyar ta ba." "Tana d'aki ai bata san muna waya da ke ba da kin ganta." Aunty ta d'aga murya ta wala mata kira, ta fito da sauri tana amsa kiran "Taho ga Hajja Umma tana niman ki." da sassarfa ta karaso inda Aunty take ta zauna gefen ta tare da kwantar da kanta a jikin ta, ido ta waro ta ce "La Hajja Umma shine tun d'azu baki neme ni ba ko." "A'a nunar gwanda bagashi na nemo ki ba yanzu, kwana biyu da ban gankiba sai naga kin dad'a kumbura, kazar turai jikin nan ya dad'a komawa tumatur sharaf." baki Feeryal ta turo ta ce "Ba Abba ya ce ya ce ki dai na fad'a min ba, ke da shi, Ammie na kashe ki kira min mijin ta muyi hira." "A waya kawai zaki ganshi ni kuma ina tare da shi a nan." "Ai baki sani ba Hajja Umma kullum sai yabi jirgi yazo gurina, ke kina can kina ta kan cewa masu aiki, kuyi kaza kuyi kaza, kar ku saka gishiri da yawa a abincin almajiran nan fa ku sa musu magi ya ji." dariya duk suka fashe da shi. Aunty ta ce "Au haka Hajja Umman take fad'a." kai ta gyad'a tana dariya ta ce "Kullum sai Abba ya shigo yace ta zauna ta huta ta barsu su suyi aikin, yana fita zata tashi taje bata zama tarika kai kawo ke nan, bata ko gajiya, ai shiyasa Abba ya ce yafi so na ma, ita kullum bata hutu gata da masu aiki." dariya Aunty tayi tana dungurin kanta. Maryam da ta shigo ta tadda suna wayan ta leko cikin wayar Feeryal ta washe baki "Aunty Maryam ina kika je ne?." "Gidan su Haulat yanzu kuwa muke hiran ki da ita, tana tambaya ta yaushe zaki dawo." "Ai nakusa dawowa, sai dai bana so na rabu da Ammie na ne." tayi maganar tana dad'a kwanciya jikin Aunty. "To ai sai ku dawo tare da Ammie'n naki." cewar Maryam tana mata hararar wasa. Wayar ta da ke rike a hannunta ne ya yi kara, ganin Miemie ce ke kiran nata yasata d'agawa. "Hello Miemie." daga cikin wayar Miemie ta ce "Feeryal yi sauri kizo kiji wani magana." "Wacce magar Miemie?." jin shiru yasata ciro wayar a kunne taga har ma ta kashe kiran. ganin Aunty sun kama wani hirar da Hajja Umma sai ta fice zuwa sashin su Miemie. Har ta kusa rabin isa sashin nasu kiran Miemie ya kuma shigowa wayar ta. "Yauwa Feeryal tsaya ma kawai bazan zo." "Ai gashi na fito ma bari na karaso." "To tsaya-tsaya ma kawai bari ni na fito." Miemie ta fad'a tare da katse kiran. Feeryal ta sauke numfashi tana fad'in "Oh Miemie." Gefe ta matsa ta jikin wasu dogayen bishiyoyin fula da suke jere a gurin, tana jiran fitowar ta. maganar da taji ta cikin bishoyoyin ne yasata juyawa da sauri ta d'an leko ta sakankanin flaws d'in. karaf suka had'a ido da Ameerah da ke zaune da saurayin ta suna hira kan kujerun da suke cikin gurin. saurayin ya mike da alama sun gama hirar zai tafi. da sauri ta d'an matsa baya. Tana tsaye har motar saurayin ya fita a gidan. a razane ta waigo jin an buga kafad'ar ta ta baya. Ameerah ta bita da kallon sama da kasa ta ce "To sannu bakar munafuka, wacce munafurcin ne yakawo ki nan kika zo kina leka min saurayi, Allah ya toni asirin ki saurayi na kike lekawa." murya a sanyaye Feeryal ta ce "Kiyi hakuri wlh bansan kuna nan ba, kuma ni ba lekensa nake yi ba." "Karya kike yi leka shi kike yi ai ina kallon ki, sai kin fad'a min uban da yasa kike lekashi, ko naci uban ki da duka anan, dama ina da cikin ki." "Allah Ameerah ni ba leken sa nake ba, ban ma san kune a gurin ba." Miemie da ke tahoto ta bud'e baki tana kallon yadda Ameerah ke d'agawa Feeryal murya ita ko sai magiya da kwantar da kai take kamar zatayi kuka. da sauri ta karaso gurin ta na fad'in "Ya ya akayi wai mene ne?." da sauri cikin tsiwa Ameerah ta ce "Kamata nayi tana leka min saurayi." Feeryal tayi narai-narai da ido ta ce "Allah ba leken sa nake ba magana naji na leka bansa su bane." Miemie ta ce "To lallai saboda Feeryal d'in ta rasa aikin yi sai ta tsaya leken saurayi kamar wacce ta rasa samari, ta ce ba leka miki saurayi tayi ba ai sai kiyi hakuri ki rabu da ita." "Karya take lekashi take yi ai na ganta da ido na." Ameerah tayi maganar cikin hayagaga. Miemie ta ce "To meye a jikin saurayin naki da za'a leka shi, ana ta ce miki kiyi hakuri kina ta wani d'agawa mutane murya to ta kalla kiyi abin da zakiyi, dalla wuce mu tafi, Feeryal tayi abin da zatayi." "To idan zan mata abun da zan matan zaki hana ne, kema bakifi karfin na had'a da ke ba bana son shishigi." Miemie ta dalla mata harara ta ce "Kar ki yadda kice zakiyi min ehe ni ba Feeryal bace kul in gaya miki, kisan wad'an da kike wa rainin wayon ki, kar ki yadda kice zakiyi min, dalla wuce mu tafi kin tsa tana gaya miki magana har kina bata hakuri." taja nannu Feeryal fuuu suka kara gaba bata fasa mitar ba. "Ki ci gaba da tsayu kowa yarika cin tuwo a kanki yana wanke kwanon, idan Ameerah ta gane kina tsoron ta to kin shiga uku bakisan wannan shegiyar bace, kin tsaya kina wani bata hakuri baki gaggaya mata magana ba, ita da saurayin nata." "To me zan ce mata Miemie jiran ki fa nake wlh ni ba leken saurayin ta nake ba." "Dalla ni ki daina min wannan maganar kayan haushin, kar kiyi baki ki iya rama waba, Ameerah da kike gani rashin mutuncinta ya wuce duk in da kike zato." shuru tayi bata ce komai ba. Kamar ko da yaushe Umma Karima ce zaune gaban bokanta, babu d'ankwali babu takalmi. a gaban su wata tukunyar kasko ce tana tafarfasa ita kad'ai tamkar yana kan garwashin wuta. boka Mali ya leka cikin tukunyar cikin kazamyacciyar muryarsa ya kece da dariya "Hahaha aiki na kan wakana sai dai har yanzu kin kasa samo cikon na uku har yanzu aikin ki bai cika ba, bazaki tab'a samun yadda kike so ba har sai kin jefa duka ukun cikin tukunyar nan." cikin damuwa Umma Karima ta ce "Boka duk yadda zanyi nayi na kasa samu babu wata hanyar da za'a bi a cikita min aiki na in yaso sai na biya kawai." Sandar tsafin sa ya buga kasa yayi wasu surkullensa kana ya zaro wata laya ya ce ya jefata cikin tukunyar nan, wani irin kumfa had'e da bakin hayaki fuuu ya taso cikin tukunyar. ya ce "Duk sanda layar nan ta gama narkewa har idan baki samo cikon na ukun ba to aikin ki ya lalace, sai dai a fara daga farko." da sauri ta ce "A'a boka hakan bazama ta faruba ko ta halin kaka zan nemo bazan bari aikin shekara da shekaru ya tashi a banza ba." "Hahaha kin yi tunani mai kyau maza ki tashi ki bazama nima." Umma Karima ta mike a bujajan tayi waje bayan ta zazzage masa bakin jaka.......! 8 Mommy ne zaune a bedroom d'in ta rike da waya a kunnen ta, tana fad'in "Ki bata hakuri Hajiya Luba halin Abdurrahim sai a hankali, ko ni nan hakuri da shi nake dole sai tayi hakuri, har zuwa san da zata shigo gidan sa bazata tab'a samin yadda take so da shi ba, dan shi wani irin mutum ne baud'ad'd'e, san da suka kasance a tare ai ita mace ce tasan yadda zata bi ta karkato da hankalin sa gare ta." Hajiya Luba ta ce "Amma dai babu dad'i haka ace an bada sadakin ka ko sau d'aya saurayin bai tab'a zuwa ba, kullum a cikin karya take wa kawayenta baya kasar ne, har wasu sun fara gane wa." "Karki damu Hajiya Luba ke dai a saka bikin nan kawai daga zaran anyi ba shike nan ba, bari alhaji ya dawo zan masa maganar ya turo aje a sa rana, ayi bikin nan da wuri kawai, kudai kuci gaba da shiri nima ina kai za'a kawo muku lefe satin aure." "To yanzu naji batu Hajiya Halima ga d'iyar taki ma wai na bata ku gaisa." Mommy ta washe baki "Ah bawa surukar tawa mu gaisa." Hajiya Luba ta mikawa Kuraiba da ke kwance a jikinta waya tana fad'in "Ga Mommy'n naku kullum in muna waya kiyi ta ce nabata ku gaisa kamar baki da wayar kiran ta ku gaisa." Mommy ta yi dariya "Yar albarka ya kike ya shirye-shirye." "Lafiya lau Mommy muna kai." "Yauwa madalla kiyi ta hakuri da Abdurrahim lokaci na zuwa." "Mommy ko na kirashi baya d'aga wayar." "Kar ki damu Kuraiba daga zaran kunyi aure duk wannan matsalolin sun kare, kinji ko." ta ce to. "Yauwa to sai anjima." Mommy ta kashe wayar. Kuraiba ta gyara kwanciyar ta jikin uwar tata. Hajiya Luba ta ce "To kinji da kunnen ki Hajiya Halima ba karamin kaunarki take ba, zaki kuma sami d'anta yadda kike so cikin ruwan sanyi." "Momma ina son Abdurrahim burina kawai na mallake shi, nadad'e ina mafarkin samin miji kamarshi, kyakkyawa kakkarfan namiji a tsaye mai kud'i." Hajiya Luba ta yi dariya tana cewa "Kud'i kam akwai shi dan kuwa su kud'i gadarsa sukayi, jinin kud'i ne a jikin su yake malala, kwantar da hankalin ki kamar kin sami Abdurrahim kin gama." Kuraiba tayi wani murmushi tana hasasho kasantuwar su da shi.. Nan da nan Mommy ta sunduma cikin soma shirin auren Abdurrahim da Kuraiba, a gefe guda kuwa Umma Karima ma na nata shirin dan kuwa ta lashi takwabi sai kanwarta Siyama ta auri Abdurrahim dan tanan ne kawai zata dad'a samin cikar burin ta. bokan ta ya bata wasu lakanin suna nan suna ta aikin shaye-shaye da shafe-shafen magani. Feeryal da Miemie ce zaune a cikin keb'ab'b'en gurin hutawa dake gefe da sashin Ammah, wanda yake a matsayin mallakin sashin, kamar yadda ko wani sashi na gidan yake da irin gurin. an zagaye fulawowi kujeru na zagaye a cikin sa gurin hutawa ne na musamman da aka kawata shi da furanni. Miemie ta bud'e baki da hanci tana kallon Siyama da ta doshi hanyar part d'in Abdurrahim. ganin yadda tayi da baki Feeryal ta saki murmushi mai sauti tana fad'in "Meye hakan Miemie?." Miemie ta yamutsa fuska tare da cewa "Dubi waccan 'yar wahalar shegiya jibeta ba gaba ba baya ba nono ba d'uwawu, gatanan tsangargar tana tafiya tana wani karairaya jiki kamar an d'aurawa muciya zane, me Ya Abdurrahim zaiyi da ita, shi da ya yi rayuwa cikin turawa da larabawa, har garama Kuraiba tana da d'an cika ita ma d'in dai ba wani fasalin kirki ne da ita ba, Mommy ce kawai ta masa dole sai ta had'a shi da 'yar kawar ta, shiyasa Hajiya ma ta ce yaje can Yelwan Shendam ya nimi mata akwai kyawawan mata a gurin, Mommy ce ta ki da Yelwa zamuje mu sha biki, da kinje garin kakanmu kin gani garin fa akwai dad'i." Da sauri Feeryal ta waiga inda Miemie take nuna mata Siyama, tana daf da shiga part d'in sa. hab'a Feeryal ta rike ta ce "Ke Miemie ki raba ni da niman magana ni dai bani da karfe idan ta jiki sai dai na gudu na barki." "Wlh wannan had'eta zanye na kalmashe 'yar banza, ai ke kin shiga uku da shegen tsoro ina abin jin tsoro a jikin waccan shamuwar mttss." taja dogon tsaki. Feeryal ta girgiza kai tana fad'in "Ni dai babu ruwa na." "Dalla ta shi mu je ki rakani na amshi book d'i na gurin Sumayya, banson kayan haushin nan naki." Feeryal ta mike tana dariya. Suka fito daga cikin gurin Miemie tana fad'in "Book d'in nan shi ke tayani hira da daddare idan bamuyi waya da Murad ba, Sumayya daga aro ta rike taki bani, kullum sai tace zata kawo min gara naje na amshi kayana, yau Murad ya yi tafiya book d'in ne zai taya ni hira." "Wani irin book ne haka, mene ne a cikin sa?." "Love story ne gobe zan baki ya kwana a gurin ki ko zaki shiga layi, dan naga ke sai an d'auraki a network kafin ki dawo saiti, jiya ma da wani abokin Ya Faisal ya ganki a sashin Ammah sai da ya tambaye ni ke, kawai na watsar da lamarin ne dan nasan ke d'in sai a hankali." baki Feeryal ta tab'e dan tana ganin soyayya duk shirme ne da kuma b'atawa kai lokaci. Suna shiga cikin side d'in Mommy Feeryal ta tsaya a farfajiya bata yadda ta shiga ciki ba. ta ce wa Miemie taje ta dawo tana jiran ta dan bata mance gargad'in Mommy kan shigo mata sashin ta ba. Da sauri Ajmal ya turo karamar kofar da ke jikin get d'in side d'in ya shigo. Feeryal ta waiga suka had'a ido ya sakar mata murmushi. itama takaitaccen murmushi ta mayar masa tare da sunkiyar da kanta. ya karaso in da take yana fad'in "A'a Feeryal ya kika tsaya a nan baki shiga ba." "Miemie nake jira ta shiga yanzu zata fito mu tafi." agogon hannunsa ya duba kana ya dube ta ya ce "Yauwa dan Allah shiga ki cewa Ameerah wai taje in ji Ya Abdurrahim, sauri nake yi ana jira na a office." da sauri ta d'ago suka had'a ido sai kuma tayi saurin sunkuyar da kanta, jiki a sanyaye ta ja kafarta, da fargabar abin da zai biyo baya idan ta shiga, tana kuma jin nauyin ta ce masa bazata iya shiga ba. Tayi taku d'aya zuwa uku ya kira sunan ta "Feeryal." cak ta ja ta tsaya tare da waigawa bata bari sun had'a ido ba kanta a kasa. numfashi ya furzar kana ya ce "Ina so muyi wata magana yaushe kike da lokaci, nazo na same ki a side Aunty." Shiru tayi tana wasa da bakin gyalen ta. "Jeki sai na dawo." ya fad'a tare da juyawa da sauri ya tafi. Takai minti 5 tsaye a bakin kofar tana tunanin shiga daga bisani ta tura kofar ta shiga da sallama a hankali. Mommy ce zaune ita kad'ai a parlour tana ganin Feeryal ta ware ido. "Ke me ya kawo ki nan?." ta fad'a tana dad'a ware ido a kanta. Feeryal taja ta tsaya jiki na kyarma. "Ke kutumar uban ki nace uban me ya kawo ki sashin nan, au anturo ki ki barbad'a wani barbad'en naku ne ko, zo nan." Mommy ta fad'a cikin tsawa. Feeryal ta zabura ta shiga takowa in da take ta tsaya gefen ta. tsawa takuma buga mata "Miko min maganin da ta turo ki ki barbad'a min, ki koma ki ce mata malamin ta ya fad'i." kai Feeryal ta girgiza cike da tsoro ta ce "Ba.ba..babu komai dama um Ya wannan ne um Ya wannan." gaba d'aya ta mance sunan shi da taji Ajmal ya fad'a da kuma yadda Miemie take kiran sa da shi. sai fad'in Ya wannan ta ke. Mommy ta ce "Da kyau mana bakuyi sammanin asirin ku zai tonu ba, dole ki rika kame-kame, hatsabibiya bakar ashana sai naci uwar ki a nan kafin naje na sami wacce ta turo kin." "Abdurrahim." taji an rad'a mata a kunnen ta, ido ta rumtse ta had'iye miyau da kyar, muryar Chuchu tajiyo a kunnen ta tana rad'a mata sunan nashi, kana ta bud'e ido da sauri ta ce "Ya Abdurrahim ne ya ke kiran Ameerah." kirji Mommy ta buga ta ce "Waye yayan naki nashiga uku! to bari kiji in gaya miki kar ki sake nasake jin kin dangana min d'a da yayanki dan shi ba yayun aljanu bane, kar ki sake nasake jin kin kira min d'a da yaya shi ba yayanki bane, kije can ki nimi yayan ki, kul nasake jin kin kira shi da yaya sai na dirza bakinki ya yi jini, wuce ki bani guri shegiya mayyar aljana." Su Miemie da suke d'aki da su Ameerah har suna rige-rigen fitowa suga wacce Mommy take wa bala'i. Miemie ta tsaya sororo tagama mancewa tare suke da ita tana jiranta a waje. jiki na b'ari Feeryal ta nufi kofa sakamakon kuma buga mata tsawa da Mommy tayi, gaba d'aya ta birkice har tana karo. Sumayya tayi saurin cewa "Gurin Miemie kika zo gata nan fa." bata ko waiga ba tuni tayi waje jiki na rawa Feeryal bakaramin tsoron tsawa da fad'a take ba nan da nan yake birkitata ta fice hayyacin ta. Ameerah ta buga dogon tsaki "Mssttt na rantse na tsani yarinyar nan bansan me yasa Daddy yaki koran ta ba." Miemie ta bita da sauri Feeryal bata tsaya ba sai da ta fice a farfajiyar side d'in gaba d'aya. ta tsaya tana maida numfashi kamar wacce tayi tsere. Miemie ta karaso da sauri murya a raunace ta na fad'in "Yi hakuri Feeryal kin gaji da jirana ne kika shigo ko, ai dama tafiya kikayi abinki baki shiga musu side ba bare ayi miki rashin mutunci, wlh na mance kina jirana kiyi hakuri dan Allah." Feeryal ta maida hawayen da suka ciko mata ido sannan ta ce "Ya Ajmal ne ya ce naje na kira Ameerah wai wannan na kiran ta, shine fa na je." "Waye wannan kuma Feeryal?." "Um wai waye sunan shi ma wannan babban yayannan naku mana wai waye ma sunan shi, am Sahab." "Sahab kuma bamu da wani yaya mai suna Sahab, Ya Abdurrahim ke nan ." "Eh shi, mamansa ta ce kar na sake ce masa yaya shi ba yayana bane, dama nima ban san shi ba." da sauri Miemie ta ruko hannun ta ta ce "Kibar maganar taho muje kiyi hakuri kinji." ta janyo ta suka yi gaba. Shirye shiryen bikin Abdurrahim da Kuraiba yana dad'a kankama, musamman a gurin iyayen su mata Mommy da kuma Hajiya Luba, a d'ya gefen har da Alhaji Jibiril wato mahaifin Kuraiba, dan yana matukar farin cikin had'a zuri'a da baban family sanannen family irin family'n A.A FIYA. Daddy ya ba Mommy isasshan kud'en da zai isa yin lefe, a b'angaren sa baya nuna farin ciki ko akasin sa game da auren. da farko shima yaso d'an nasa yaje gida can Yelwan Shendam ya nimi mata, amma da Mommy ta buga kasa ta kekashe ita tayi masa mata sai ya kyale ta, tun da ita uwa ce ita ma tana da hakki a kan sa, sannan kuma ya d'an yaba da gidan da matar ta fito. Dubai Mommy ta tafi suka had'e da Hajiyan Dubai bayan sun had'a akwatuna set biyu suka wuce Egypt suka had'a set uku kafin ta biyo girgi da kayan ta dawo. sashin Hajiya aka jibge kayan, 'yan'uwa da abokan arziki ana ta zuwa gani, anata yaba kyau da tarin yawa da tsada irin na kayan. Feeryal da ta fito daga bathroom d'aure da towel, ta isa gaban wardrobe da sauri ta bud'e gefen da su pant da pat d'in ta suke. ido ta d'an waro tuno da pat d'in ta ya kare ga period d'in ta ya zo. dafe goshi tayi tana fad'in "Wayyo na mance ashe ya kare." sai kuma ta rufe wardrobe d'in tayi waje tana fad'in "Ammie Ammie." a sakiyar parlour suka had'e da Aunty da kiran nata yasata fitowa daga kitchen. "Ya akayi ne Feeryal mene ne da irin wannan kiran?." baki ta turo tare da langwab'ar da kai cikin muryar shagwab'a ta ce "Ammie pat d'ina ya kare." ido Aunty ta waro gaba d'aya ta mance da tame d'in period d'in ta ya yi, dan ko wani tame tana zuwa duba pant da pat nata, tagama mancewa da wancan watan pat d'in zai kare bazai kai wannan watan ba. ta ce "Subhanallah na gama mantawa ne amma bari Baba Rabi yanzu ta fita taje ta siyo miki, jira yanzu za'a kawo miki." Aunty ta juya da sauri ta koma kitchen in da suke aiki da Baba Rabi. ita kuma ta juya ta koma d'aki. Ta kasa zama sai sintirin shiga bayi take tana wanke shi da ruwa, sam bata son jini ya b'ata mata jiki ko kad'an, a rana takanyi amfani da pat kusan goma dan duk san da zataje fisari to fa sai ta canza pat. gaba d'aya ta damu tana jin ta kamar a kan kaya take, da sauri ta d'au hijabi ta zura kan towel d'in jikin ta, ta fita da sauri ta nufi sashin su Miemie. A parlour ta tadda Ammah ita da Faisal. ta gaishesu tare da tambayar Ammah Miemie, Ammah ta ce "Tana sashin Hajiya." "Wayyo Allah." ta fad'a a kasan ranta a fili kuwa cewa ta yi "Ammah bari na d'auki abu a d'akin Miemie." Ammah ta yi murmushi tana cewa "Ke da d'akin ku har sai kin fad'a zaki shige shi." itama murmushi tayi. Faisal kuwa cewa ya yi "Kar dai Miemie ta koya miki halin gulmar nan nata." nan ma murmushi tayi ta wuce d'akin. wardrobe d'in ta ta bud'e ta bincika ko zataga pat tagama dube-duben ta bata gani ba, abin haushin ma ga wayar ta a kan gado bata tafi da shi ba bare ta karb'i wayar Ammah ta kirata da shi tun da itama bata fito da wayar ta ba. kamar zatayi kuka ta fito. Amma ta ce "Kin sami abin ko ta canza masa gurin ajiya, kin san halin ta da iya b'oye abu kamar me." d'an jim tayi tana jin nauyin ta ce ga abin da take nima ga Faisal a gurin, sai kuma ta girgiza kai ta ce "Zanje na dawo kafin ta dawo." Ammah ta ce "Ko zakije ki kirata acan tazo ta baki, Miemie idan ta sami hira ba dawowan yanzu ba, bare anje ganin kayan lefe." Feeryal tayi shiru bata isa taje sashin Hajiya ba kam. maganar Amma ta kuma ji "Kije ki kirata Miemie fa bazata dawo yanzu ba." a hankali ta juya ta fita, kamar kwai ya fashe mata a ciki a haka ta isa kofar Hajiya. ganin tsayuwa bazai ficceta ba tayi jahadi tasa kai ciki. Mutane da yawa cikin parlour'n da wanda ta tab'a gani da wanda bata tab'a ganin su ba. an baje kaya cikin parlour' kamar masu shirin bud'e ShopRite. gaba d'aya mutane tun shagala da kallon kayan sai santi suke. har ta karaso ciki babu wanda ya lura da ita, tana ta baza ido dan ta ga ta ina Hajiya take, amma bata ga ko walkiyan ta a parlour'n ba. da sauri ta isa in da Miemie take tsaye tana ta d'aga kaya tana aikin zuba surutu. ta tab'a ta ta baya, bige hannunta tayi tana cewa "Dalla barni kai gawani arnen sarka wayyo Allah na." Feeryal ta kuma tab'ata, sai sannan ta juyo baki ta washe ta ce "La Feeryal ke ce dama na d'auka Nabila ce take tab'ani ta nuna min wani abin, ke zokiga kaya dan Allah wai duk wa mutum d'aya za'a kai." hannu Feeryal ta yarfe ta ce "Dan Allah Miemie ba wannan ba taho muje ki bani pat nawa ya kare Baba Rabi taje siyo min bata dawo ba." "To naji zauna bari na gama ganin wannan akwatin." ta turata kan kujerar bayan ta, ta zauna tab'as a kan kujerar. tana kokarin ta shi ta kuma mai data "Dan Allah ki tsaya na gama gani muje na baki." Miemie ta zauna kan hanun kujerar tayi banga banga da kafafunta ga mutane ata gefen ta babu ta yadda zatayi ta mike. "Miemie muje ki bani dan Allah sai ki dawo." bata ko jinta hankalin ta nakan magana da kallon kaya. Ya kosa da jin maganar Hajiya da Mommy ta kawo karar sa gurin ta, kan yaki zuwa su tattauna yadda shagalin bikin nasu zai kasance da amaryar tasa. ya mike daga kan kujerar da yake zaune cikin d'akin Hajiya da ta gama zuban ta baya ma jinta idanun sa yana kan waya, ya mike yana d'an jan gajeren tsaki ya zura takalmansa. ganin tafiya zaiyi Hajiya ta ce "Kai abokin turawa maza kaje gidan su yarinyar nan kar ka sake baka je ba na gaya maka ke nan, in banda abin ka ana son yi maka gata ma dube ka fa gabjeje da kai ace baka da iyali, sa'anninka duk sunyi aure da 'ya'ya uku hud'u, dubi d'an nan Isa d'an gidan bappanku Jibo matansa biyu da 'ya'ya shida, gasu nan dugui-dugui tafe da kafafunsu, tafiya na Yelwan nan na ganshi cikin 'ya'yan sa gwanin sha'awa, kuma sa'anka ne, sai yaushe ne zakayi auren kai idan aka barka haka zakayi ta zama babu aure, ina kuwa uwarka zata so, itama zataso ganin 'yan jikokin ta kamar yadda nake ganin ku nake jin dad'i." Kofa ya nufa yana fad'in "Ko naje ko banje ba aure ai bazai fasu ba, to kuyi mana kawai, me zai sa sai naje." yayi waje yana d'aga kiran da ya shigo wayarsa." Hajiya ta d'aga murya tana cewa "Ai aure kamma kamar anyi an gama baza'a cigaba da zuba maka ido ka cigaba da zama tuzuru ba." Da sauri ta waiga jin ana jan abu akan kujerar da take kai. caraf idanunta ya sauka cikin nashi. wani irin mugun fad'uwar gaba ne ya ziyarce ta zuciyarta ya yi wani irin tsalle kamar zai faso kirkinta ya fito. da d'a gimtse fuska ya yi yana gyara rukon wayar da ke kunnensa, ya yin da hannunsa guda ke rike da rigarsa da ke kan kujerar da Miemie ta turata kai.........! 9 Da karfi ta janye idanunta daga cikin nashi wanda kad'an yarage ta kwalla ihu tsabar tsoro ga wani irin mashahuriyar kwarjinin dake cike cikin idanun nasa. da sauri ta kalli inda hannunsa yake yana kokarin jan rigarsa a kan kujerar da take zaune a kai. da sauri ta wani irin zabura ta mike tsaye jiki na kyarma. ya d'ago rigar yana mai ware idanunsa a kansa, ya yin da fuskarsa ya dad'a sauyawa izuwa na b'acinrai karara. ido Feeryal ta ware kan rigar da sauri ta dafe kirjinta dake ta tsalle yana niman hanyar fita, numfashin ta na sarkewa tagama sadakarwa fita zaiyi ya bar gangar jikin ta. bata ankara ba taji ya jefo mata rigar kan fuskarta tare da jan dogon tsaki "Mssttt stupid wawuyar kazama." kana ya juya ya fice a parlour'n. hanu na rawa ta ciro farin rigar daga kan fuskarta, wanda jini ya yi makeken shati a jiki. tana rarraba ido cikin parlour'n sai dai babu wanda ya lura da abin da ya faru kowa hankalin sa na kan kallon kayan da suke kallo. Da sauri ta bubbuga Miemie ta juyo. tuni hawaye yasoma sauka a idon ta, Miemie ta ce "Feeryal mene ne kuma?." rigar ta d'ago ta nuna mata murya na rawa ta ce "Ina ta ce miki kizo mu je gashi kinsa na b'ata masa riga." ido Miemie ta waro ta ce "Wannan kamar rigar da Ya Abdurrahim da ya shigo da shi a hannunsa, dan singlet ne kad'ai a jikin sa sai wannan rigar dake rike a hanun sa ya shigo, ya wuce d'akin Hajiya kafin shigowar ki." kai ta gyad'a hawaye ya zubo sharr. Miemie ta ce "Munshige su yi sauri muje mu wanke kafin ya fito ya gani." cikin Feeryal ya dad'a d'ura ruwa cikin muryar da kuka ke son kwace mata ta ce "Ai ya gani." kirji Miemie ta dafe da sauri ta jata sukayi waje, sai da suka fita kafin ta ce "Da gaske yafito ya gani?." kai ta gyad'a hawaye na zuba. Miemie ta rike kugu tare da sauke numfashi sannan ta ce "Muje mu wanke masa da sauri." Feeryal ta gyad'a kai jiki na rawa suka wuce sashin Ammah. Suna shiga d'aki Miemie ta ce taje bayi ta gyara jikin ta, tad'u pat da sabon pant ta bata da kaya ta saka. tafito ta rab'e bakin gado tana ciccire ido, ganin yadda ta tsorata da yawa Miemie ta shiga bata baki tana fad'in bazai mata komai ba ta saki ranta ai ba da gangan tayi ba, kuma ma ai ita ce da laifi, ita ta sata zama kan kujerar da rigarsa ya ke kai. ta shiga bayi ta wanke masa rigarsa tas da ruwan kumfa mai kamshi, kana ta sarkakeshi da ruwa mai kyau, yafita kwal babu ko d'igon jini, kana ta wanke towel da hijabin da Feeryal d'in ta cire. ta matse a inji ya boshe ta fito da su. ganin yadda rigar ya yi haske bazaka tab'a ce wani abu ya same shi, nan Feeryal tad'an ji sanyi cikin ranta. Miemie ta kuma fesa turare har kala uku a jikin rigar sannan ta jona ayon ta goge shi ba rigar ba hatta cikin d'akin gaba d'aya ya garwaye da kamshi. Miemie ta d'ago ta dubi Feeryal da ta d'an fara dawowa hayyacin ta ta ce "Yauwa to muje a kai masa." Feeryal tayi raurau da ido "Miemie bazai duke ni ba?." "Babu abin da zai miki muje to ni zan kai masa imma dukan ne ni ya duke ni." Suka fito Feeryal na jan kafa da ka ganta kasan a mugun tsorace ta ke. can suka hango sa bakin get na side d'in sa yana tsaye jikin motar da alama fita zaiyi dan ya sauya shiga, wani riga da wandon yadi ne skai blue d'inkin haf jamfa a jikin sa, ya yi matukar kyau cikin shigar, murjajjen fatarsa Chocolate colour sai d'aukar ido ya ke. Miemie ta tsaya da sauri ta dubi ta ce "Feeryal dole fa ke zaki kai masa, karb'a ki kai masa ki bashi hakuri, nasan idan nakai masa zaice kin rainashi me yasa ke baki kai masa da kanki ba." nan da nan Feeryal ta dad'a birkicewa har sai da taji wani jiri ya gilma mata. "Yi sauri ki kai masa kinga zai shiga mota." Miemie ta damka mata rigar a hannunta. "Je ki mana Feeryal kar ya tafi." numfashi ta fizga da kyar kana ta soma d'aga kafarta, jikinta na rawa ta kankame rigar gam-gam kamar mai shirin b'uya jikin rigar, jikin ta na b'ari da kyar take iya d'aga kafarta tana tafiyar sand'a, gaba d'aya jikinta kyarma yake, yanayin tsoron da take ciki bazai misaltuba. da kyar ta isa in da yake, kasan cewar fuskarsa na ta jikin mota ne ya bata baya. nan ta sami damar iya tsayuwa ta bayansa, da kyar ta iya bud'e baki murya na rawa had'e da sarkewa ta miko masa rigar tana fad'in "Ka.ka..kayi hakuri ga.ga..rigarka." Da d'an sauri ya waigo da alama baisan da mutum a gurin ba ga yadda ya juyo d'in, wani irin dibirbircewa tayi kamar ta kurma ihu ko ta ruga aguje. sanda idanunta ya sauka cikin nashi. sabar tsoro sai da rigar ya sub'uce a hannunta ya fad'i kasa. Ido ta waro tare da kai hannun ta duka biyu ta toshe bakin ta, sai kuma tayi saurin sunkuyawa ta d'au rigar ta rungume shi a jikinta gam-gam. ido ya bita da shi fuskarsa babu annuri. kai ta shiga girgizawa tayi baya da kafarta ta shiga ja da baya murya na rawa ta ke fad'in "Dan Allah kayi hakuri." wani kallo ya wurga mata tare da cewa "Move here!." ya juya ya shige motar sa yayi wa motar ki ya nufi babban get. Da sauri Miemie ta fito daga mab'uyarta ta zo in da take da sauri ta ruko ta tana cewa "Feeryal bai karb'a bane?." kai ta gyad'a mata hawaye sharr. Miemie ta ce "Ai dama da wuya ya karb'a taho muje kawo rigar bazai kuma sawa ba zan baiwa Isa direba" Ganin yadda Feeryal d'in ta birkice gaba d'aya, Miemie ta rakata sashin su, suna shiga Miemie ta juya, ita kuma ta shige bedroom d'in ta ta haye can kuryar gado ta dunkule guri guda ta cusa fuskarta cikin blanket. Miemie na fita tayi gurin Isa direba ta kai masa. Isa direba ya yi ta murna ganin riga mai kyau da tsada. kasancewar war yau asabar ne su Ajmal suna gida, akan idon su tayiwa Isa direba kyautar rigar. zata koma Faisal ya kira ta, ya ce ta zo ta kaiwa Ammah kulan ta. ta karaso gurin su. Faisal ya mika mata kular yana fad'in "Ke a ina kika sami rigar can da kika bashi." "La ai bansan kuna nan bama da kai na kawo mawa, ko kuma ba kai bama Ya Ajmal ko Ya Shamsuddin." Faisal ya harareta "Ke ni sa'anki ne." Ajmal ya yi dariya ya na fad'in "A ina kika sami irin wannan rigar haka, ko saurayin ki ne ya kawo miki tsarabar nashi." "Cap waya bashi kud'in siyan wannan rigar, a ina ma taga saurayin tukun." cewa Faisal yana hararar ta. Shamsuddin ya ce "Wa ya fad'a maka wad'annan yaran ai sai Allah duk suna da samaruka, ranar ma ina jin Sahla wai tana hira da saurayi a waya hmm." dariya ta yi tana cewa "Rigar Ya Abdurrahim ne fa dan mun samasa datti a jiki shine wai baya so, shine nikuma na kawa Isa direba kyautar sa, ban san kuna nan ba da ku na kawo muku." "Yauwa idan kuka kuma yin datti da wani ya ce baya so ku kawo min, wai ina mutumiyar taki ce yau na ganki ke kad'ai." cewar Shamsuddin. ta ce "Yanzu muka rabu tana side d'in su, Ya Shamsuddin kana so Ya Abdurrahim yayi mana kabarin da ba sallah ke nan idan muka kuma sa masa datti a jikin kaya, tap hmm." ta juya da sauri ta bar gurin.. Tun da Feeryal ta kule d'aki bata fito ba tana nan a dunkule cikin bargo tsabar tsoro har wajen magriba tana kwance, kan kace me jikinta ya had'a zafi rau zazzafan zazzab'i ya saukar mata. Ganin shiru-shiru Aunty bata ji d'uriyarta ba, nan ta tuna da tun d'azu taga shigowar su da Miemie, Miemie ta fita ita kuma ta shige d'aki, bata kuma ganin ta ba tun daga lokacin. Aunty ta nufi bedroom d'in ta na kwad'a mata kira. ta tura kofar ta leko kanta ciki, can ta hangota kwance dunkule cikin blanket tana rawan sanyi. Da sauri Aunty ta iso bakin gadon tana fad'in "Subhanallah Feeryal lafiya me ya same ki?." ta hayo gadon tare da zame blanket d'in taji jikin ta zafi rau kamar wuta. hankalin Aunty ya yi mummunar tashi, nan da nan ta d'aga waya ta kira family doctor su. ya ce mata ya fita ya yi nisa amma zai dawo zuwa anjima zai zo. Aunty ta ce "Dan Allah Dr ka taimake ni kazo yanzu." "Hajiya kiyi hakuri zan iya kaiwa awa d'aya a hanya ma kafin na iso kinsan yanayin garin akwai gosulo da yawa, kuma na d'anyi nisa wlh amma dai zan iso ko zuwa bayan isha ne in Allah ya yarda, a bata paracetamol ta sha kafin na iso." Aunty ta kashe wayar ta mike da sauri ta je d'akin ta ta d'auki paracetamol da ruwa ta dawo ta d'agota ta tallafo ta tana fad'in "Sannu Feeryal sannu kinji, baki da lafiya shine zaki kwanta kiyi shiru da ciwo na cinki, sha maganin nan kafin Dr ya zo." Rau-rau tayi da ido sai ga hawaye masu d'umi sun zuba, cikin galabaitaccen murya ta ce "Ammie kar yamin Allura dan Allah Ammie kice kar ya min Allura." "Kiyi hakuri Feeryal kinji jikin ki kuwa, nasan ma dole sai an had'a da allura kafin ya yi sanyi, sannu kin ji, ina ne ke miki ciwo yanzu? sha maganin maza yanzu kafin ya zo." Ta saka mata maganin a baki had'e da ruwa ta sha tana matsar kwalla. Aunty na zaune a gefen ta tayi mata pillow da cinyarta, sai sannu take jera mata. ko da lokacin sallah ya yi a nan d'akin nata tayi al'wala tayi sallah. har wajen karfe tara Aunty na zuba idon ganin Dr ganin goma saura ta kuma kiran sa a waya. ya ce gashi nan a hanya gosulo ya tare shi. Aunty tayi salati ta rasa ina zata sa kanta sabar damuwa. ga shi Daddy baya nan. a haka suka kwana tare da ita, jikin ya d'anyi sanyi ba sosai ba sakamakon paracetamol d'in da ta sha. kusan asuba jikin ya kuma yin zafi rau sai rawar sanyi take. Aunty ta rasa ina zata sa kanta shalelen ta ba lafiya. Ana idar da sallar asuba ta kira number Dr sai dai akayi rashin sa'a wayar akashe. tayi ta kiran number har gari yayi haske, ganin hakan ba zai samar mata mafita ba. tayi waje da sauri tana kwad'awa direba kira. sanin yanzu suna masallaci ta yi waje da sauri. Abdurrahim ta hango yana shigowa da alama daga masallaci ya fito, da sauri ta tare shi tana cewa "Dan Allah Abdurrahim ka taimake ni Feeryal ba lafiya kaje ka duba ta, kwana tayi bata rumtse ba, jikin ta ya yi zafi sosai, ina ta kiran Dr tun jiya har yanzu bai zoba, ka tai maka dan Allah." d'an jim ya yi ganin irin magiyar da take masa ya ginjina kai alamar zai je. da sauri ta juya ta koma ciki, shi kuma ya wuce side d'in sa yana shiga ya haye gado ya kwanta......! Mommyn Twins ce 10 Ganin shiru-shiru bai zoba Aunty ta kira sa a waya. kiran wayar ne ya tashe sa daga baccin da ya fara. gajeren tsaki yaja, kana ya mike zaune ya yi mika tare da yin salati. ya zura takalmansa ya mike tsaye ya ja bedside ya d'ibi abubuwan da zai bukata ya zura cikin aljuhun jallabiyar jikin sa, kana ya fita ya nufi sashin Aunty. a bakin kofar parlour suka had'u ta fita zuwa da kanta ta kira shi. da sauri Aunty ta juya tana cewa "Yauwa Abdurrahim dan Allah ka duba min ita." baiyi magana ba yabi bayanta dan yana mugun jin nauyin ta. Feeryal na kwance cikin bargo. Aunty ta hayo gadon tana cewa "Feeryal ta shi ga shi za'a duba ki, karaso dan Allah Abdurrahim." ta janye bargon, idanun ta a lumshe bawai ko dun tana bacci ba sai dan jirin da take ji. a sannu ya toko d'akin hannayen sa suna nad'e a kirjin sa. ya karaso bakin gadon, kallo d'aya ya yi mata ya d'auke idanun sa. a hankali ya sauke hannayen sa da suke nad'e a kirjin sa. kana a sannu yakai yatsun sa biyu kan goshin ta. patt!. haka taji kirjinta ya buga san da yatsar sa ya sauka kan goshinta, da kyarfi ta rumtse idanunta tare da jan numfashi. Ya janye hannunsa tare da zurashi cikin aljuhu ya zaro allura ya fasa ya zuko shi cikin Syringe. "Gyara Feeryal ayi miki allura ba sai kin tashi ba a kwancen ma za'a iya yi ko Abdurrahim." Aunty ta fad'a tana duban shi. kai ya gyad'a batare da ya yi magana ba. wani irin zabura tayi jin an ambaci sunan allura. murya na rawa ta ce "Aa Ammie ni dai bana so kar ayi min." had'iye ragowar maganar tayi ganin shi tsaye a gaban ta. hannu takai ta mussuke idanunta zaton ta gizo ne. jin Aunty tana cewa "Ke ki tsaya da'alla abin da ba zafi Abdurrahim yi mata kaji." huf ta mike tsaye ta tsaya da kafafunta a kan gadon, ta matsa can karshen gado tana yarfe hannu da fad'in "Wayyo Allah Ammie naji sauki kar a min." "Ke dalla bana son shiririta kina b'ata masa lokaci fa." ta janyo ta ta zille tare da fashewa da kuka tana yarfe hannu "Ammie dan Allah dan Allah Ammie kar a yi min naji sauki ma." ta rika yarfe hannu tana buga kafa kan katifa. Aunty ta ruko ta da karfi, ihu ta fasa tana tirjewa. gajeren tsaki ya ja cike da kosawa ya mika hanu ya fisgo ta ta fad'o kan kafar Aunty, ta rirtike ta, itama ta kankame ta gamgam tare da b'oye fuskarta jikin Aunty. tsaki ya kuma ja badun nauyin Aunty da yake ji ba da babu abin da zai sa yazo bare har a tsaya ana masa wannan haukar. kwafa ya yi afili Aunty ta fahimci ransa ya b'aci, ta bugawa Feeryal tsawa "Idan baki tsaya ba za'a barki da ciwon ki kiyi ta fama, kina hauka ne allura kawai kamar cire ran ki za'ayi haba dan Allah, yi hakuri Abdurrahim kayi mata." ta d'an ja sket d'in ta kasa Baki ya tab'e ya d'an matso ya nitsa allurar ta saman pant d'in ta. kara ta kurma ta kai hannu ta rike nashi da ke rike da allurar ya bige hannuta bayan ya matse ruwan allurar ya zare shi a jikin ta, yana mai dad'a gimtse fuskarsa, ya cika har wuya. da kyar ta tsaya a ka kara mata d'aya, "A sa mata ruwan sanyi a jikin ta." ya fad'a a takaice. Aunty ta d'ago ta a jikin ta ta sauka ta shige bayi da sauri. Feeryal kukan allura har da majina. ganin Aunty ta shige bayi itama ta mike da sauri ta duro a gadon. tana d'aga kafa taji abu ya cake ta a bayan hanu. kara ta kwalla tare da d'ago hannun tana yarfe shi. wani kallo ya wurga mata sannan ya saki allurar dake hannunsa kasa, "Stupid girl." ya fad'a kana ya juya ya fice a d'akin Aunty ta fito da sauri tana fad'in "Feeryal lafiyar ki tun da an gama ina shike nan ko sai kin tsaya shiririta, me ya sami hannun naki kike tallafe shi sai kace a hannun aka yi miki allurar." Aunty ta ruko hannun nata tana cigaba da cewa "Um kin gani karin gardamar ki har kin ji ciwo a hannu gashi har ya d'an fidda jini, sannu zauna na sa miki towel zaki dad'a jin dad'i, jikin naki ya yi zafi sosai baki ji ya ce asa miki ruwan sanyi ba." Feeryal bata iya magana ba sai matsar kwalla take. Aunty ta taimaka mata ta cire kayan jikin ta, ta d'auko mata wani riga bes da wandon sa iya guiwa ta saka, kana ta rika jika towel tana shafa mata a jikin ta. har sai da taji jikin ya yi sanyi kafin zuwa lokacin kuwa bacci ya d'auke ta. Aunty ta fita taje ta kama aiki akai-akai take shigowa dubata, sosai jikin ta ya yi sanyi ta jima sosai tana bacci.. "Ya shugaba na akwai tsoron wani mai tsanani a tare da ita, gata a kwance cikin jinya sakamakon tsoron nashi." waziri Kutup ya yi maganar yana zubewa gaban sarki Aljani Matip tare da d'aura ruwan madubin ganin zahiri daga rayuwar ta bisa kafar sarki Aljani Matip. kura mata ido ya yi sosai sannan ya ce "Aje a wanke mata fuskarta da ruwan zuzirr, akwai bak'in yana da magauta masu neman ta sukayi jifa ya fad'o fuskarta, shi yasa idan tayi duba a gareshi firgici yake dirar mata, a wancan lokacin malam Buba Mani bai san da ragowa a goshin ta ba, wan da ya gani kawai ya iya cirewa." kasa waziri Kutup ya yi da kansa yana cewa "A gafarce ni ya shugaba na amma me yasa sai a kansa take shiga wannan yanayin, ga sauran bil'adam kuma ba haka ba." murmushi sarki Matip ya yi sannan ya ce "Magauta bincike suke babu dare babu rana sun watsa taurarin su ta ko ina domin cikar burin su, tauraru ya fad'a a kansa duk da hasken shi ya disashe taurarun su amma yana tasiri a jikin sa, shi yasa take jin hakan game da shi, a wanke mata fuska da ruwan zuzirr na karkashin teku, ganin da zata kuma yi masa zai kona taurarun su dake razanar da ita, wanda yake a matsayin tarko gare ta, za'a shafe sammanin su da suke jin sun kusa gado inda take, duk da taurarun nasu baya da kaifin tasiri a kanshi, har yanzu lalub'e suke cikin duhu." "Na d'auki umurni ya shugaba na." Waziri Kutup ya mike domin isar da umurnin da aka masa.. Sai bayan sallar la'asar ta farka. tana bud'e ido ta saki murmushi ganin Chuchu da Chulu a kusa da ita. Chuchu na rike da hannunta tana share mata d'an guntun jinin da ya fito kan bayan hannunta. mikewa ta yi ta zauna tana fad'in "Laa Chuchu Chulu kunzo ne har kun dawo daga tafiyar?." suma murmushin suka mayar mata, Chulu ta ce "Dawowar mu ke nan, muka biyo nan, baki da lafiya kinji sauki ko mu baki magani." "Naji sauki kaina ke min ciwo kad'an kad'an yanzu." wani d'an karamin tandu mai murfi ta ciro, ta kwance marfin ta ce "Kawo hannun ki na zuba miki ki wanke fuskarki zaki ji kan ya dai na miki ciwo." ta mika hannu ta tsiya ya mata har sau uku tana wanke fuskarta da shi.. fuska ta yamutsa tana kallon hannunta dake rike a hannun Chuchu sannan ta ce "Wannan Sahab d'in nan ne ya caka min allura a gurin." Chuchu ta ce "Kina so ki rama?." ido ta d'an waro ta ce "Tsoro yake bani kuma duka ya ke yi fa, baku ga yadda ya yi wa su Miemie ba." "Ki dai na tsoron shi ba ga munan ba zamu taya ki, idan ya ce zai duke ki zamuyi mishi irin na Mommyn shi, kin mance tun da data tab'a dukan ki muka rike mata kafa ta kasa iya tafiya, to haka zamuyi masa shima." Dariya ta fashe da shi tuno da abin da suka tab'a yi wa Mommy tun tana karama. sai da dariyar ta yi tare da cewa "To amma ai kunce shi kun kasa iya yi masa komai, shifa mugu ne baku ga yadda ya caka min allura ba." "Ina abin da muka baki ki sa masa a jikin san nan?." "Yana can cikin wardrobe nifa tsoro nake ji, a ina ma zan ganshi na saka masan." "Duk in da kika ganshi ki san yadda zakiyi ya tab'a jikin sa, ta nan ne kad'ai zamu sami damar iya yi masa wani abu, idan ba haka ba to mu ba zamu iya yi masa ko mai ba ba zamu iya zuwa jikin sa ba, mun d'au ki wancan a in da kika ajiye, amma zamu baki wani." d'an shiru tayi tana tunani ta ya za a yi ta iya hakan. "Babu abin da zai miki ki daina tsoron sa mu zamu taya ki kinji." kai ta gyad'a. Chulu ta mika mata wani jan ganye guda d'aya ta ce "Idan wannan ya tab'a jikin sa zamu iya zuwa jikin sa, bai isa ya yi miki wani abu ba zamu rama miki." ta karb'a tana murmushi nan take ta kudiri aniyar saka masa a jiki, duk da bata san ta in da zata fara ba. Har kusan magariba suna tare sai da Aunty ta shigo tashinta ta tashi magariba yayi tayi wanka, kafin su Chuchu suka tafi. Kasancewar tana fashin sallah, tana fita daga wanka ta saka kaya ta fito parlour. Aunty taji dad'in ganin yadda ta warware sosai, kamar ba ita ce jiya da d'azu abin tausayin nan ba. Suna parlour da Aunty na sallar magriba ita kuma tana kwance tana buga game a wayarta. Miemie ta shigo, ta zauna gefen ta tana fad'in "Mara lafiyar ke nan d'azu na shigo ai kina bacci Aunty ke ce min baki da lafiya." murmushi ta yi "Eh amma naji sauki." "Ba dai tsoro ne ya saki ciwo ba,ma tsoraciya kawai." dariya kawai ta yi. Miemie ta zauna sukayi ta hira har bayan sallar ishe kafin ta koma sashin su. Siyama ce ta fad'o cikin d'akin Umma Karima, ta cire takalmi mai tsinin da ke kafarta tayi wurgi da shi. "Ya ya mene ne hakan Siyama?." "Aunty Karima kiyi wani abu dan Allah, ki duba fa ki gani lokaci kurewa ya ke dad'a yi, auren nan fa da gaske za'ayi, gashi duk wata hanyar da zanbi wai dan hankalin sa ya dawo kai na duk a banza, dubeni ki gani dubi shiga ta ki gani ki ga irin had'ewa ta fa, a haka yazo ya iske ni a sashin Mommy amma ko kallo ban isheshi ba, duk yadda zanbi na janyo hankalin sa na bi amma babu wata nasara." Umma Karima ta mike ta dafa kafad'ar ta ta ce "Ina so ki kwantar da hankalin ki, kar ki damu zaki mallaki Abdurrahim zaki same shi a tafin hannunki, boka yabani tabbaci kuma yana kan aiki a kan haka, na yadda da boka Mali nasan bazai wasa mana kasa a ido ba, auren nan da ke za'ayi in har ina numfashi." "Aunty Karima in har abin nan bazai yuwuba kawai ni zan tinkare sa, na fad'a masa ina son sa." "Dalla matsa can mashirmaciya kawai shi zai zo da kansa yace yana son ki, kuma zaki sha mamaki ki zuba ido kawai ki gani." Da sauri Umma Karima ta d'aga hannu a kafad'ar ta tana cewa "Tsaya ma tukun wai nikam kamar naga sonshi da gaske kika fara." a dibirbirce Siyama ta ce "Kamar ya Aunty Karima ai ni so nake ayi-ayi musamu abun da muke bukata, naga jinkirin zuwan lokacin ne kawai." "Ai ho yanzu naji batu je ki ki cire kayan nan ki huta, ki kwantar da hankalin ki kamar tsumma a randa, kamar yanzu lokaci zaiyi ayi a wuce gurin." Siyama ta sauke b'oyayyen numfashi kana ta tattari takalmarta ta yi d'akin su. Feeryal ce kwance a parlour saman doguear kujera rike da waya tana buga game. Miemie ta shigo ta zauna gefen ta tad'a mata buka acinya tana fad'in "Yanzu dama wayar tana hannunki nake ta kira kika ki d'aga wa." "Wash Allah Miemie ta zafi fa." "Ai dama so nake kiji zafin, ayi ta kiran ki a waya kike d'agawa, tun d'azu na tura miki abu ta Whatsapp baki ma hau online d'in ba bare ki gani, ke kam ma ba amfanin wayar ki, kalli kiga ni ashoben da muka cire na kannen ango kala biyar ne, Unaisa da Umaima'n Hajiyan Dubai ne zasu taho mana dashi daga can, duk kalolin nan ba karamin kyau zasu miki ba." ta karb'i wayar tana duba wa "Gaskiya sun yi kyau kam." ta fad'a tana mika mata wayar. Miemie ta ce "Ai sosai ma kuwa idan muka yi waya da su zance a siyo har da ke." "Da ni kuma to ai ni ba kanwar ango ba ce me zai sa nayi ashoben." Miemie ta tsare ta da ido. kai ta gyad'a tana cewa "Eh ai Mommy ta ce shi ba yaya na ba ne kinga kuwa ni ma ba kanwar sa bace." "Dan ta fad'a shine me dalla kiyi abin ki, kowa zai sa ke ne bazaki saba." Feeryal ta d'au wayar ta ta cigaba da buga game d'in ta tana cewa "Meye a ciki tun da ba tsirara zanyi yawo ba, nifa bazanyi ba karma ki sa su kawo." Aunty da ta fito daga kitchen tayi shiru tana sauraran su. Miemie ta mike tana cewa "To idan an kawo an d'in ka kar ki sa." "Ki sa a kawo da ita zata saka ma." cewar Aunty tana karaso wa cikin parlour'n, Miemie ta ce tom kana ta dubi Feeryal da ta tab'e fuska. Tana cewa "Goben zamuje gyaran gashin kuwa ni fa so nake ma ayi min kitso gashina sai karyewa yake gara naki shi baya komai, kar gashin yagama gwaguyewa." "Eh zamuje." "To Allah ya kaimu." ta fice ta koma sashin su. Washegari da wuri Miemie ta gama shiri ta biyo wa Feeryal suka fito bayan Aunty ta gama yi musu kashe din su dawo da wuri. suna hanyar su na zuwa parking lot Ameerah ta hange su. murya ta d'aga "Ke Miemie tsaya-tsaya-tsaya." Miemie ta juyo tana dalla mata harara dan tasan bai wuci halin nata na rashin mutunci zatayi mata ba. Ameerah ta karaso in da suke ta harare su sama da kasa sannan ta ce "Da kika cewa su Unaisa su karo ashobe na mutum d'aya, ke zaki sa kala goma iri d'aya da naki da wanda za'a karon." "Ina ruwan ki meye damuwar ki idan zan sa duka, idan kuma ma wata zan bawa kina da matsala ne, ko akwai sisin ki a cikin kud'in siyan kayan, Daddy ne me bada kud'in ko ke da kika titsiye ni kina tambaya ta." "Ai nasan bai wuce ma wannan Aljanar kika sa ba, to tunda kud'in bana uban ta bane baza a kawo da ita ba, ta had'a dangi da Ya Abdurrahim d'in ne da zatayi ashoben bikin sa, to bama son gayyan sod'i, ta tsaya a matsayin ta dangin sa ne zasuyi ashoben bikin sa ba bare 'ya'yan tsintuwa ba." Feeryal tayi murmushin takaici taja hannun Miemie ta ce "Muje Miemie." Miemie ta fisge hanun tana cewa "Ke kam kin yi asara Ameerah haka zaki kare da gori, idan kikace zakiyi min ni wlh farfasa miki baki zanyi 'yar rainin wayo." "Miemie muje dan Allah, ki rabu da ita." Feeryal ta fad'a tana kuma ruko ta. Ameerah ta waiga gefe da sauri ta isa bayan mota ta sunkuya ta d'auko magen Hajiya da ke kwance a gindin mota, ta jefawa Feeryal a jiki tana gad'in "Munafuka idan bata rabu da ni ba ya zatayi da ni." Wani irin uban ihu Feeryal ta kurma tare da kankame jikinta dake cirawa, nan da nan kwayar idanunta suka sauya, tayi wani irin yanke jiki ta rid'u a kasa, tare da kuma kwalla kara ta zare gyale da d'ankwalin kanta ta yamusa gashin kanta. tayi wani irin mikewa ta shako wuyan Ameerah.........! 11 Wani irin damka tayi wa wuyan Ameerah, tana wani irin gurnani. idon Ameerah ya firfito, ta d'aga hanu kafafaka kamar kaza a cikin ruwa ta rike hanun Feeryal tana ja tayi-tayi ta iya b'anb'are hannunta a wuyan ta ta gagara. ganin yadda Ameerah ta ke fafutukan niman numfashi, da sauri Miemie ta ce "Sake ta Feeryal yau kin nuna mata shiru shiru ba tsoro bane gudun magana ne, kyale ta mu tafi wannan ya zame mata darasi in ita mai gane wa ce, in kuma bata gane ba gaba a kuma ankarar da ita." da sauri Miemie ta shiga kokarin janye ta, sai ji tayi kamar dusi take tab'awa. "Feeryal kyale ta sake ta haka." tafad'a tana jan hannunta dake wuyan Ameerah, amma ko gizau hannun ta baiyi ba. da sauri ta dube ta cike da mamakin yadda taji takasa iya b'anb'are hannunta dake wuyan Ameerah. da karfe ta d'ago kanta dake sunkuye gashin kanta ya rufe fuskarta. a razane Miemie tayi baya ganin kwayar idanunta da suka sauya izuwa na ban tsoro. Da gudu ta juya tana fad'in "Me gadi security Feeryal Ameerah kuzo dan Allah wlh ba ita ba ce ba Feeryal ba ce!." gaba d'aya ta kid'ime, tayi bakin get a guje tana kiran security. Nabila da Sahla da komai ya faru a kan idon su dan tare suke da Ameerah dama, su suka tsaya jiranta ita kuma ta karaso ciwa su Miemie mutunci. suka juya da gudu sukayi sashin Mommy suna fad'in "Wayyo Allah Mommy Feeryal zata kashe Ameerah." Mommy ta fito a hargitse dai-dai sanda Security suma suke karasowa gurin. Aunty ma ta iso a bujajan Baba Rabi ta sanar mata da abin da ke faruwa. Security suka bugawa Feeryal tsawa sukace ta sake ta. ganin bata da niyyar sakin ta, ga yadda numfashin Ameerah ke yi kamar zai bar jikin ta, suka shiga kokarin jan Feeryal da jan hannunta a wuyan ta. amma ko gizau basu iya ko da jijjigata ba. Mommy ta ce "Wayyo Allah shegiya mayya zata kashe min yarinya." tayi kukan kura tashiga dukan Feeryal da hanu bibbiyu ta baya tana fad'in "Mayya sake ta kashe ta zakiyi." wani irin sa kafa tayi ta baya ta angiza Mommy sai ga Mommy a kasa shirim, ta kawo ihu ta saka, tana dafe bayanta. security hud'u sukayi kan Feeryal sukayi sukayi su iya kwace Ameerah a hannunta suka kasa. Aunty da hankalin ta yayi mummunar tashi ta zo ta gaban Feeryal tana fad'in "Kuyi hakuri dan girman Allah ku sake ta na gama ku da Allah, kar ku ja mana masifa." "Ai ita ce masifar babban annoba wayyo Allah mun shiga uku zata kashe 'yar gida, wayyo jama'a ku kawo mana d'auki za'ayi kisa." Umma Karima da rahoto ya kaimata ta iso yanzu take fad'a. ta ci gaba da fad'in "Ku harbeta da bindiga idan bata sake ta ba, kuna gani zata kashe ta, dalla ku kashe mara amfani." sai kuma ta juya da gudu tayi sashin Daddy tana ihu. Ta fad'o cikin parlour'n Daddy tana fad'in "To Alhaji gashi can za'ayi kisa a cikin gidan ka, ka aje gamasheka ta bunkasa tafara cire wuyan 'yan gida, ga mayyar Aljanar 'yarnan can ta makure wuyan Ameerah har jini na fita, ko numfashi bata yi wata kila ma ta mutu yanzu, wani irin bala'i ne wannan ka ajiye mana a cikin gida." Daddy ya dubi Umma Karima da take haki d'ankwalin ta a hanu ya girgiza kai, kana ya gyaza zamansa ya d'aga kafarsa d'aya ya d'aura kan d'aya sannan ya dubi, Abdurrahim dake zaune a gefen sa kasan Carpet ya ce "Abdurrahim je ka suna fad'a ka rabasu." "Alhaji ka taso kaje ka ganewa idon ka kasheta fa zatayi." Daddy ya d'au tsiririn gilashin sa ya saka sannan ya d'au jarida ya bud'e yakuma gyara zamansa yasoma karantawa. Abdurrahim ya mike ya nufi waje domin isar da umurnin da Daddy ya basa. Umma Karima ta bi bayan sa da gudu tana cewa "Yauwa Abdurrahim yi sauri kafin ta kashe ta tun da shi ya ki zuwa bare ya d'au mataki, gata can zata kashe maka kanwa 'yar autarku, mayya ce fa taki sakin ta." bai kula ta ba yaci gaba da tafiyar sa. Mommy na baje a kasa tana kururuwa ta kasa ta shi. Hajiya ta fito kafa ba takalmi, tana ganin hanun Feeryal a wuyan Ameerah tasa hanu a ka ta kawo ihu ta saka, "Wayyo Allah zata kashe min jika, me kuka tsaya yi baku nemo itace kun buga ma 'yar banza ba, ku d'auko itace ku jinke ta da shi, kuna gani zata kashe ta, wayyo Allah na shiga uku zata kashe min jika." Hajiya tayi kan Feeryal da duka tana jan rigarta. "Sake ta bazaki kashe min ita ba gayyan tsiya yau zaman ki ya kare a gidan nan." bata rufa baki ba ta jita a kasa bip ta ture ta. Hajiya ta yi kururuwa tana cewa "Ni Abukabar zai kawo abin da zata kashe ni da jokikina a gidan nan." Aunty ko hannu bibbiyu ta had'a tana roko da magiya had'i salati. security kuwa suna ta kokuwan b'anb'are hannun Feeryal a wuyan Ameerah da jikin ta ke b'ari numfashinta na sama-sama. babu makogoron yin ihu. Suna ganin sa suka sake ta suna cewa "Sir akwai matsala fa, ina ga sai an kira liman ya mata rokiyya, mun kasa cire hannunta a wuyanta." "Abokin turawa ku had'u ku jata ku fidda ita a gidan nan, ku kai ta can cikin ruwa ya tabbata wannan 'ya ba mutum bace, ina zan iya da gayyar tsiya, bazata kashe ni ta kashe min jikoki ba." fuska ya dad'a murtukewa tare da gyara tsayuwarsa ya saka hannunsa a kafad'arta ta baya ya fizgota, ya fincikota ta da karfi tayi tangal-tangal ta zube kasa. Ameerah ma ta fad'i kasa tare da sakin wahallen kara tana dafe wuyanta. Feeryal tayi wani irin mikewa tare da calla kara tayi kan Ameerah dake kasa tana rike da wuyan ta, Aunty tayi saurin shiga sakanin su tana fad'in "Haba ku kuwa bakusan girman Allah da manzon sa bane, me yasa kuke irin haka." tuni ta kauce ta gefen Aunty ta mika hanu tana kokarin kuma shako Ameerah, ya sa mata kafa ta fad'i kasa rip. ta kuma calla kara ta shiga birgima a kasa tana bige-bige, can kuma ta mike flat gaba d'aya jikin ta ya sake, tashiga mai da numfashi. Aunty ta yi kanta tana jijjigata da kiran sunan ta. Da sauri Hajiya tayi kan Ameerah ta rungumo ta tana duba wuyan nata Mommy ma ta zo ta rungume ta na dudduba jikin ta. Hajiya ta ce "Sannu kinji Ameerah Allah ya isa miki sai ta bar gidan nan taje can ta karata, haka kawai so take ta kashe ki kina zaman zaman ki tazo ta same ki ta shakure miki makogoro anya ma ba turo ta akayi ba, dan ta had'a kai da 'yan ta'adda dama, to wlh ba a gidan nan ba, ina ji ina gani bazata kashe min jika ba, ke Fatima d'auki tsiyar ki kisan yadda dare ya yi muku." Miemie da tun d'azu take hawaye da sauri ta ce "Hajiya wlh ba laifin Feeryal ba ce, zamu tafi gyaran gashi ne Ameerah ta tsare mu tarika zagin ta, takuma d'auki kyanwa ta jefa mata a jiki, kuma tana tsoron mage." Abdurrahim ya yi tsaki ya juya ya bar gurin. Mommy ta ce "To ai dole taji tsoron mage tun da ba gaskiya a lamarin ta, bazan zuba ido a cutar min da 'ya ba sai na d'auki mataki." "Matakin ke nan yanzu-yanzu ta bar gidan nan." cewar Umma Karima. Hajiya ta ce "Ai dama kam zama ya kare mata a gidan nan dan gobe bamusan wa zata kuma cirewa makogwaro ba, kuje ku kira min Abubakar, sannu kinji 'yar nan tashi muje zai zo ya same ni." Hajiya ta d'ago Ameerah da bakin nan nata ya mutu murus, suka tafi sashin ta. Mommy ma ta koma nata shashin bayan ta gama zazzage bala'i. Umma Karima ta juya kan Aunty dake ta kokarin ganin Feeryal ta dawo hayyacin ta. tana ta aika mata habaici. bata ma san tana yi ba burin ta d'iyarta ta dawo hayyacinta, tana ta tofa mata addu'o'i. zuwa can ta dawo gayyacin ta, da taimakon Baba Rabi suka tallafe ta suka tafi da ita side d'in Aunty. Dole Daddy ya je kiran da Hajiya take ta ai ka masa. ta in da take shiga batanan take fita ba, dole Feeryal ta bar gidan. Daddy ya ce "Hajiya ai ba laifin yarinyar ba ne idan kika duba Ameerah ita ce me laifi, yau duk Miemie ta fad'a min irin tsokanar da Ameerah take mata kuma bata tab'a ramawa ba, kuma yau d'in ma ai ba ita ce ta rama ba mutanen kanta ne suka tashi, sakamakon abin da bata so take tsoron sa ta jefa mata mage a jiki, Hajiya duk ki bar maganar nan sab'ani ne kawai irin na yara, idan aka fiye magana irin haka sai na rikajin ciwo na kamar zai tashi, yarinyar da ta kusan tafiya ma." Hajiya ta walalo ido Daddy ya yi maganar da bata son ji game da lafiyar sa. "To to ai shike nan amma irin wannan shaka da tayi mata kamar zata kasheta, in yazo da sautsayi ai sai ya tafi da rai, amma Abubaka kana ma shan maganin ka kuwa, Kulu kira min Ajimi yaje ya kira min abokin turawa, yazo ya duba ka imma zai baka wani maganin ne du yazo ya baka, ai yazo da sauki ma tun da yana gidan." "Hajiya ba damuwa zan je na same shi dan naji kirjin na min zafi." "Yi maza hanzarta kaje ka same shi, ina amfanin tara mutane a gida hankali na tashi in kaga yaya kaje can Yelwa ka huta ka bar musu gidan." Daddy ya yi waje. Hajiya ta dubi Ameerah tana cewa "Ungo karb'i ki sha ruwan sanyin nan, zakiji wuyan naki ya yi sanyi, ai takusa ta tattari tsiyarta ta tafi kowa ma ya huta." Ameerah ta karb'i ruwa ta shanye tana maida numfashi. "Jeki kiyi wanka ki rire wad'annan kayan da sukayi kuran ki sauya wasu, zan sa abokin turawa ya baki magani." Ameerah ta mike bakin nan mud'us ta koma sashin su. Ameerah na zaune a parlour kusa da Mommy tana cin abinci bayan tayi wanka, Ajmal ya shigo ya dube ta yana zama kan kujera ya ce "Ke Ameerah wai kije in ji Ya Abdurrahim." baki ta turo sannan ta aje plt d'in abincin ta mike ta fita. A parlour'n shi ta iske shi zaune ya d'aura kafa kan d'aya. Laptop na kan cinyarsa yana latsawa. d'an nesa da shi ta tsaya ta ce "Gani Ya Abdurrahim." "Zo nan." ya fad'a yana nuna gabansa tare da sauke kafafunsa kasa ya aje Laptop d'in saman table, ya gyara zaman sa. Ameerah ta ja kafa tazo gaban sa, tana waige-waigen ganin ko akwai wanda zai ceceta kusa dan tasan babu tuntub'i sai ta sha dukan da bata san laifin ta ba. a gaban sa ta sunkuya tana wiki-wiki da ido. ya d'au belt a gefen sa, tana kokarin gudu ya janyo ta sai da ya yi mata bulala goma kafin ya sake ta, yana cewa "Idan kika kuma sa ta sake d'aga mana aljanu a gida, ta tara mana jama'a sai na d'aye miki fata, Stupid Get out." Ameerah ta mike da gudu tayi waje tana kuka. Da kuka ta fad'o parlour'n Mommy da sauri Mommy ta mike tana fad'in "Kuma tare ki tayi zata kashe ki?." cikin muryar kuka ta ce "Ya Abdurrahim ne ya bige ni." "A wani dalilin laifin me kikayi tun baki dawo daga jinyar da aka d'aura miki d'azu ba." "Ai tasan laifin ta shegen niman magana ne da yarinyar nan, ina ruwan ta da Feeryal me ta tsare mata a gidan nan, kullum ke kenan niman tsokana, ai da fasa miki jiki ya yi sosai ta in da gobe bazaki sake niman wata yarinya da tsokana a gidan nan ba." cewar Ajmal yana hararar ta. Mommy ta rike hab'a ta bud'e baki "Au dama akan ta ne yamiki wannan dukan, bayan kashe ki da ta so yi." "To Mommy ko ma me ai ita ta jawo." "To shanyayye ai dama kai da shi kamar wa Hajiya Fatima na haifa mata, duk ta lashe ku ta barbad'a muku magani cikin abinci." Ajmal ya mike ya fita yana hararar Ameerah........! 12 Tun daga ranar Aunty ta hana Feeryal fita ko nan da can, ko da Miemie ta zo sai dai su karaci hirar su a nan ta tafi. jin guri shiru hajiya bata kuma cewa ko mai ba, hankalin Aunty yafara kwanciya. Tuni shirin biki ke dad'a matsowa, uwar ango Mommy da uwar amarya, Hajiya Luba ba zama, ana ta shirin yadda biki zai tafi ta yanda baza a ji kunya gun kawaye ba. tuni gidan Alhaji Abubakar A.A FIYA yafa d'aukar baki 'yan biki dangi na nesa da na kusa. Su Hajiyan Dubai da 'ya'yan ta Umaima da Unaisa, suma sun hallaro. Kamar yadda Mommy ta fad'a satin aure za'a kai lefe, aure na da sati guda ke nan su Hajiyan Dubai da wasu dangin Mommy da Daddy da kawayen Mommy suka kai lefe gidan amarya. abun da ya yi mugun tadawa Siyama hankali ganin irin tulin kayan da aka kaiwa Kuraiba. a haukace ta shigo d'akin Umma Karima, Umma Karima tana zaune tana waya da bokan ta. Siyama ta shiga kai kawo cikin d'akin ta kasa zama. "Boka a maganar da nake maka saura sati d'aya fa bikin nan, sai yaushe ne za'a wargaza auren aure saura kwana kad'an. boka ka taimake ni kar kabari ayi auren nan." "Maganar waya bazata yi ba kizo kiji binciken kaddarar ki." "To to gani zuwa ni dai buri na naji daddad'an kaddadar bincike, dan Allah boka a zurfafa bincike, sai nazo." Umma Karima ta sauke waya ta dubi Siyama tana fad'in "Akan ido na aka fita da kayan nan bakin ciki ya hanani fita, ta turo nazo muje kai kaya nace ace mata yau na tashi da ciwon kai, boka ya ce nazo ya yi bincike ya gano wani abu, zan je naji dan nasan bazai bamu kunya ba." "Aunty Karima kin ga kayan kuwa ashe Hajiyan Dubai ta kuma zuwa da wasu, cikin mota uku fa aka tafi da shi, ban da wan da suka saka a sauran motocin da suka tafi." "Ke duk wannan ba wani abu bane in zamu sami abun da muke so nawa ne wannan kayan da bai wuce kud'in shan shayi ba, ki natsu cip zan je naji me boka zai ce." Umma Karima ta mike ta zari mayafi ta fita. Umma Karima zaune gaban boka Mali ba mayafi ba d'ankwali ba takalmi ta nad'e kafa kamar mai niman gafara. boka Mali ya d'ago ya dube ta bayan yagama zane-zane da buga kasa ya ce "Akwai yuwuwar yin auren nan babu yadda za'ayi dole sai anyi sa, idan kuma aka matsa wajen hana yiwuwar sa to wasu aiyukan zasu iya rushewa, musamman aikin cikin tukunyar can shima zai iya tarwatsewa." ta girgiza kai da sauri "A'a boka bana son aikin can ya rushe zan iya hakura ayi auren, amma bazan iya jure rashin wancan aikin ba." "Hahahaha kinyi nazari mai zurfi." ta mike tana fad'in "Yanzu boka babu wani d'an taimakon da za'a iya yimin, amma dan Allah kar ya tab'a aikin can." "Bazamu iya yin komai ba yanzu ki bari ayi auren." "Nagode ubanmu maganin kukan mu idan ina bukatar wata taimako zan dawo dan kai ne kad'ai mai iya share min hawaye, duk abin da na nima na samu in kana numfashi Allah ya kara tsoron rai." Ta fice daga cikin kogon inda ko da yaushe take tub'e mayafi da d'ankwali da takalmin ta ta isa, ta d'auka ta saka kana ta karasa gurin mota in da direban ta ke zaune cikin mota yana zaman jiranta. ta bud'e gefen mai zaman banza ta shiga ta zauna sharap. Liti direba ya dube ta yana fad'in "Ina muka dosa hajjaju?." gajeren tsaki ta ja ta ce "Mu tafi hotel gaba d'aya yau raina a b'ace yake." "An gama ranki shidad'e." yaja motar suka nufi in da ta umurcesa.. "Feeryal yi sauri dan Allah mu tafi, idan fa bamu je mun zaunawa telan nan bafa ba bazai mana d'inki kan lokaci ba." "Miemie wai dole kuma sai munje bayace zai kawo da kansa ba, mu jira mugani ko zaikawo anjima." "Ke baki san halin teloli ba ne, ba ga su Sahla sunje sun amso nasu jiya ba, kuma ai duk tare ya ce zai kawo mana, me yasa bai kawo mana ko ya basu su kawo mana ba, muje kawai mu amso muma." Feeryal ta mike tana gyara gyalen abayar jikin ta, ta saka takalmi mara tudu suka fito. A can jikin get d'in side d'in Hajiya suka hangi Hajiyan Dubai da su Unaisa. Miemie ta ce "Taho muje Feeryal ga Hajiyan Dubai can yanzu sai tace mun ganta bamu zo mun gaishe ta ba, shegen son a gaishe ta matarnan ko me gaisuwar yake badawa oho mata." Tun kafin su karaso Hajiyan Dubai ke bin Feeryal da kallo har suka karaso. a tare suka had'a baki wajen gaishe ta ta amsa tana dad'a karewa Feeryal kallo "Lafiya lau sannun ku." har sun juya zasu tafi Hajiyan Dubai ta ce "Ke Miemie a ina kika samo wannan, ko cikin ba'in Lebanon ne da suka iso." "A'a Feeryal ce yarinyar Aunty." "Wacce Aunty wai Hajiya Fatima, Aunty naku yaushe ne ta haihu bamu sani ba, au kar dai ace 'yar da ta tsinto d'in nan ce." Umaima da Unaisa da suke jingine jikin mota dukansu rike da waya suna latsawa, da alama fita zasuyi da uwar tasu, sai a lokacin suka d'ago suka kalli Feeryal. Unaisa ta d'an yi murmushi "Miemie sannun ki." Miemie ma guntun murmushin tayi mata. dan tasan halin su ko wannen su d'an ji da kai ne suna ganin sun fi kowa, suna rayuwa a Dubai. ta ce "Sannun ku kuma Feeryal muje ko." cewar Miemie tana jan hanun ta. "Yanzu ke Miemie baki jin kishin kanki, kina yawo da wacce ta fiki, taya za'ayi saurayi ya ganki ya ganta ya d'auke ki a kanta, ni sam bana son yarinyar data fiye kyau haka tana huld'a da 'ya'ya na, ita uwar taki ma bata san me take yi ba da ta zuba miki ido ta barki kuna yawo tare da ita." Miemie bata ce kala ba ta ja Feeryal sukayi gaba, tamkar basuji me take fad'a ba. Acikin mota ne Miemie ta dubi Feeryal da jikin ta ya d'an sanyi. ta ce "Hm matar nan fa duk bakin ciki ne ya dame ta, dan taga saura kad'an Ya Abdurrahim ya yi aure, ai da ta so had'a shi da Umaima shi yaki." Hmm kawai feeryal ta ce tana juya lamarin cikin ranta. Ko da sukaje suka samu telen ya gama d'in kin su, babban shago ne da ma'aikata da yawa, har zasu tafi d'aya daga cikin telolon ya ce musu ga sauran kayan Ameerah su tafi mata da shi. Miemie ta ce bazasu karb'a ba tazo da kanta ta karb'a, ai suma da suka zo suka karb'i sauran kayan su basu karb'a musu nasu da aka gama ba. Feeryal ce ta karb'i kayan suka nufo gida Miemie na ta mita. "Yarinyar da ba a yi mata gwanin ta ba burgeta zakiyi ba." "Nima ba so nake na burge ta ba, kawai taimako nayi yiyyar yi mata." Miemie ta yamutsa fuska. Suna isa gida Miemie ta dubi Feeryal tana cewa "To ai sai ki kai mata tun da wulakanci bai ishe ki ba dan ni dai bazan kai ba." "Ni ma ba zuwa zanyi ba zan dai baiwa masu aiki su kai mata." tana rufa baki suka hango ta ita da su Unaisa da Umaima Sahla Nabila Sumayya, sun fito daga sashin Hajiya. "Muje daga nan ki mika mata mu wuce." suna zuwa sashin Mommy su suna tafiya sashin Aunty a tsakiya suka had'e. Sumayya ta ce "Yauwa Miemie Hajiya ta na niman ki." "To daga gun d'inki nake sai na je na ajiye kayana kafin naje, me zata min ma tukun." Sahla ta ce "Ina zamu sani mu, yauwa ya gama miki d'inkin duka kuwa? mu ma can zamuje mu amso sauran kayan Ameerah." "Ya gama duka har da na Feeryal, d'in ki ya zuba kyau sai kowa ya saka a tantance, Feeryal mika mata kayan ta, gashi nan ta karb'a mata." laidar kayan Feeryal ta mikawa Ameerah da tayi gum da bakin ta kowa yana magana ita bakin ta a suke kamar ruwa ya shanye ta. sai cika da basewar da take ita fa a dole boss ce a cikin su. ta amshi laidar har lau bata ce kala ba ta soma tafiya. Unaisa ta dubi Feeryal ba yabo ba fallasa ta ce "Feeryal sunan ko ba laifi kam akwai kyau." takaotaccen murmushi tayi mata. Nabila ta ce "Mujen ku dan Allah." suka bi bayan Ameerah suka nufi sashin Mommy. Miemie ta juya tana kallon bayan su, dariya ta tuntsure da shi tana cewa "D'an iska na kauye sai tsoron d'an'sanda, dubi Ameerah yadda ta nutsu, karyar iskanci take, duk shan kwayar ka ai akwai wanda ya d'are ka, gargad'in ya shige ta ke nan." Feeryal ta bita da ido dan bata fahimci abin da take nufi ba.. Ana saura kwana uku biki Farida da mijin ta suka duro Nigeria da baby girl d'in su mai suna Neezrah. sun kuma dawo akan dai-dai kab'ar da mijin nata ya kammala aikin da ya ajiye shi a Uk. gida ya cika makil da 'yan'uwa da abokan arziki. in da tuni sabbin ma'aikatan da Mommy ta d'ibo damin bikin suka had'e dana gidan suka cigaba da d'aura manyan tukwane suna sauke wa. Dr Imran ne ya shigo bedroom d'in Abdurrahim cikin shigar sabbin kaya masu kyau. tsayuwa ya yi cikin d'akin yana binsa da kallon mamaki ganin sa kwance, yana baccin sa cikin kwanciyar hankali. Da sauri ya karaso bakin gadon yashiga bubbugashi yana fad'in "A.A wai bacci ka wanta yi a wannan lokaci? ai kai da bacci sai bayan biki, dalla tashi ga ba ba'i can suna jiran ka." tsaki ya ja "Wai meye haka ne kam Imran ina ruwan ka da bacci na." "Da ruwa na mana taya za'ayi ma ka kwanta bacci ne kam, to ko ni nan tun baccin jiya da daddare da na tashi da asuba ban kuma komawa ba har yanzu, bare kuma kai uban gayyar da kanka, mutanen Germany fa sun iso gana Abuja ma, ko wanne nasa an musu masauki a hotel daban daban, ya kamata ka tashi kaje ku gaisa dan kai fa sukayi tattaki suka zo, musamman ma wad'an da suka taho daga wata kasar." Kwafa ya yi tare da mike wa zaune yana aikawa Dr Imran mugun kallo "Amma nace ban yarda ka gayyaci ko wanne daga cikin su ba ko." "Au da so kake sai dai suji kayi aure, haba su da kullum suke maganar Allah ya kaisu ranar auren ka, nasan suna yi maka fatan kar ka mutu tuzuru ne, suma jajayen fata sukayi aure a kan lokaci bare kai da ka fisu kwari da lafiya, taso kaje kayi wanka ka shirya da'alla mu tafi, kar ka mance dai 8:30 na dare akwai kamu kuma kasan dole zamu je." Tsaki yaja ya mike ya nufi bathroom yana fad'in "Ai sai ka jani ka kai ni." Kafin ya fito Dr Imran ya zab'ar masa kaya cikin sababbi kuma tsadaddun d'inkunan da Daddy ya yi masa. ya feshe su da turaruka masu dad'i da sanyin kamshi. ya d'auko hula da takalmin da zasu shiga da kayan suma duk sababbi ne, ya aje masa su kusa. yana fitowa ya ce "Yauwa yi maza ka hanzarta ga kayan da zaka saka." baiyi magana ba sai hararar sa da yayi. ya wuce gaban mirror ya zauna ya d'au Body lotion yasoma shafawa fuskarsa a murtuke. Dr Imaran ya ce "Yi da jikin ka mana kayi ka sa kaya." ta cikin mirror ya hararesa "Kai kafa dame ni ba maganar ka ce zata sani fita ba, sai dun kada wad'an can mutanen da ka gayyato su suce sunzo kasar mu anyi musu wulakance, badun haka ba babu abin da zaisa na katse bacci na." "Eh na dai ji tun da zakaje ai shike nan karb'i kasa." ya mika masa kayan. sai da ya kuma hararar sa kafin ya amsa ya saka. tun kafin ya gama shirin ai nihin kyansa da cikar halittarsa da kwarjinin sa had'i da cikar haiba suka bayyana a gare sa. kayan ba karamin amsar kalar fatar sa wankan tarwad'a ya yi ba. sai wani sheki fatarsa chocolate color keyi. ya d'aura tsadadden agogo a tsintsiyar hanunsa kana ya murza huta a kansa, ya zura takalmi a kyawawan kafafunsa masu d'auke da zarazaran yatsu da fafaren farce. Dr Imran ya bud'e baki da hanci yana kallon sa, sai yau ya dad'a ganin ainihin sagwaran kyansa a fili. duk da shi ba fari bane amma ko kyawawan fararen fatan da suke kasashen ketare, basu isa su nuna masa ko mai ba. ganin yadda Dr Imran ya bud'e baki da hanci yana kallonsa. yaja tsaki ya zari makullin mota ya yi waje. da gudu ya biyo sa na fa d'in "Innalillahi kai ka ganka kuwa had'uwa iya had'uwa, wlh aure rahama ce tun ba'a d'auraba har ka kara kyau." Bai kula shi ba ya yi gaba. sai da yafito harabar side nashi ya dubi parking lot nasa, yaga motoci hud'u ne a ciki, makullin motar daya d'auka kuma ya mance jiya ya faka motar a babban parking lot na gidan. gajeren tsaki yaja, sam baya son fita cikin gidan ya had'u ma da kowa, sai dai kuma ya fito baya son kuma komawa. haka ya nufi get d'in sa badun ya so ba, Dr Imran ya rufa masa baya. Ai kuwa yana fita hankalin jama'a ya dawo kansa. aka sunkuya masa kirari irin na ango. Dr Imran kuwa sai washe baki yake yana d'agawa mutane hannu, har suka isa parking lot. ya jefa ma Dr Imran key'n motar, ya cab'e yana cewa "Ai dole na tuka ango." ya shiga mazaunin direba shi kuma ya zauna d'aya gefen, Dr Imran ya yi wa motar key mai gadi ya bud'e musu get. Suna fita hotel in da aka sauke 'yan Germany suka fara nufa. yaga ko mai an tanadar musu na bukata ya yi musu barka da zuwa, ya zauna suka d'an tab'a hira, kana suka fita suka je d'aya hotel d'in da aka sauke ma'aikata likitocin su na Abuja. suma an tanadar musu komai na bukata, bayan d'an hirar da sukayi da su ma. kana yasa Dr Imran ya dawo da da shi gida. Suna shiga gida ana kiran sallar magriba. dan haka suka sauka suka nufu masallaci, sai da akayi sallar isha kafin suka shigo gida. yana shiga bedroom d'in sa yashiga rage kayan jikin sa. Imran ya karaso yana cewa "Yauwa A.A yi wanka ka sauya kaya da sauri kaga time na zuwa kamun nan ya yi, na gayawa Dr Sharif da Dr Taj mu had'u a can, bai kyautu ace bamu je musu ba." "Kai nifa babu in da zani, ka dai na cika min kunne zaka iya tafiya dan bacci zanyi." yana kaiwa nan ya shige bayi bai jira jin amsar sa ba, tun da ya shiga kuwa bai fitoba. Dr Imran yasan sarai so yake ya tafi kafin ya fito. ya lekashi ta jikin glass d'in kofar bayin, ya hango sa kwance a cikin bathtub daya cika sa da ruwa. idanunsa a lumshe. kai ya girgiza ya juya ya fita dan yasan dama da kamar wuya yaje. yaje ya had'u da sauran abokan nasu suka tafi gurin kamun........! *Nima ina da biki yau da gobe da jibi sai kuyi hakuri bazaku ji ni ba sai an gama, kafin nazo muje mu leka bikin Abdurrahim da amaryar sa Kuraiba*πŸ€— 13 Ahankli ya bud'e idanun sa da suke a lumshe ya mike ya fice cikin bathtub d'in. ya ja towel ya d'aura a kugun sa ya fito. ya tako zuwa in da fridge ya ke ya d'au gorar ruwa mai sannyi ya bud'e ya kai bakin sa, ya kusa san rabin gorar sannan ya mayar da ragowar. ya tako izuwa gaban wardrobe yabud'e ya ciro gajeren wando da singilet ya saka, ya isa gaban mirror ya feshe jikin sa da turaruka masa dad'i da sanyin kamshi kana ya fito parlour. Ya haye kan doguwar kujera ya kwanta tare da d'aukar rimut ya sauya tasha izuwa MBC2. Ajmal ne ya shigo da sauri had'e da sallama, ya karaso cikin parlour'n ya d'an rusuna tare da sosa bayan keyarsa "Bar ka da dare brother." da kai ya amsa shi yana d'an kallon shi ganin kamar da magana a bakin shi. Ajmal ya dad'a sosa bayan keyarsa yana fad'in "Am Ya Abdurrahim dama so nake so ka d'an bani hula nawa sunyi datti sauran suna gurin wanki." "Je ka d'auka." yafad'a a takaice. da sauri Ajmal ya ce "Godiya nake bro." ya wuce da sauri cikin bedroom d'in nasa ya zab'o hula cikin tarin hulunar sa yafiyo yana washe baki, da gwada hular a kansa, har ya hango had'uwar da zaiyi da wannan tsadadden hular. yana fita ya dad'a yi masa godiya bakinsa ya kasa rufuwa, har ya isa bakin kofa zai fita ya kira sunan sa. "Ajmal je ka karb'o min Sudan tea a gurin Aunty." ya ce to. da sauri ya fice yana duba agogo tara saura. kuma karfe goma amarya Kuraiba ta ce masa za'a tashi a hall d'in, gashi sai kiran sa take yazo-yazo, dan tasan yayan nasa kam ba zuwa zaiyi ba, so take shi d'in yazo ta b'adda kafa gun kawayen ta. Da sauri ya shigo parlour'n Aunty d'auke da sallama a bakin sa. Aunty na kichin ta fito tana amsa sallamar nasa. "Aunty barka da dare." "Yauwa barka dai Ajmal " "Aunty wai inji Ya Abdurrahim wai ki basa Sudan tea, amma dan Allah Aunty ki d'ansa wani ya kai masa, wlh sauri nake tun d'azu amarya take ta kira na, gashi ko wanka banyi ba bare na shirya." Aunty ta ce to. "Yauwa Aunty nagode." da sauri ya juya har ya kai kofa ya juyo "Aunty dan Allah kar ace ban tsaya na karb'a ba, ace natafi ne zan dawo in karb'a da aka gama kuma aka kai masa kafin na dawo." Aunty ta yi dariya. shima dariyar ya yi kana yafita da sauri. Aunty ta koma kichin da sauri, dan girkin Daddy take yi. Nan da nan ta had'a masa Sudan tea ta zuba shi cikin Mug kana ta fito. d'an jim tayi da tunanin wa zai kai masa, gashi Baba Rabi ta gama aikin ta ta koma b'angaren su na masu aiki. kira ta kwad'awa Feeryal ta fito tana amsa kiran. "Zo ki kaiwa Abdurrahim tea d'in nan yanzu ki dawo, babu wanda zai kai masa, yi sauri girki na zai kone." d'ankwalin material d'in kanta ta warware tayi mayafi da shi, kasan cewar yana da d'an girma, kana ta karb'i Mug d'in. Aunty ta koma kichin tana cewa "Kina kai masa ki dawo." har ta nufi kofa ta tuna da abun da su Chuchu suka bata suka ce ta sa masa ya tab'a jikin sa. ta juya cikin sand'a ta na kallon kofar kitchen gudun kada Aunty ta ganta. ta shige d'aki ta isa in da ta aje ganyen da suka bata silli d'aya ta d'auka, har yanzu yana nan kore sharr d'in sa. ta fito da sauri tayi waje. magana taji a bayanta ta juya da sauri sai kuma ta saki murmushi. ganin wad'an da suke bayan ta. "Ai mun d'auka kin mance da abun ne, ashe kin tuna muje to mu rakaki." suka soma tafiya tana cewa "Na tuna ai ko na saka masa cikin tea d'in ne.' "Aa kar ki sa a ciki jikin sa kawai muke so ya tab'a." kai ta gyad'a dai-dai san da suke fitowa daga sashin Aunty. Cikin gidan tamkar rana hasken wuta ta ko ina, mutane ba'i 'yan biki suna ta zirga-zirga, bazakace dare bane. a sannu suka isa bakin get d'in b'angaren nasa. Chuchu da Chulu suka ce "Anan zamu tsaya ki shiga muna jiran ki, kar ki bari ya gani kisan yadda zakiyi yad'an tab'a jikin sa kawai." "Amma dai bazai duke ni ba ko?." "Har yanzu tsoron sa kike ji ne?." "Da ne yake bani tsoro da yawa amma yanzu ba sosai ba." "Yauwa to ai gamu a nan kina sa masa zamu iso in da yake, bazamu bari ya yi miki ko mai ba." "Kun tabbata dai ko?." kai suka gyad'a mata. ta tura karamar kofar ta shiga, tsayuwa tayi tana karewa side d'in nasa kallo, wan da tun da take gidan bata tab'a shiga ba. iyaka ta hangi get d'in da ido. plat ne guda biyu a cikin side d'in gefe da gefe sai Upstairs a tsakiyan su, amma kusan a had'e suke. shima farfajiyar side d'in lungu da sako kamar rana ko ina hasken wuta wanda ko allurar ka ne ya fad'a kasa zaka ganshi. tsayu tayi tana tunanin ta ina zata fara. a hankali ta soma d'aga kafarta tana nufar sakiyan wato kofar parlour'n kasan Upstairs d'in in da take hango window sa a bud'e ga kuma iska na d'aga labulen window. Tana isa bakin kofar ta gyara rukon tea d'in hannunta, kana tayi knocking d'in kofar. tad'an tsaya kad'an kana ta kuma yi har sau uku a jere. a hankali ta kai hannunta kan handle ta murd'a ga mamakin ta sai taga ya bud'e. numfashi ta sauke a hankali a sannu ta zura kafarta ciki bakin ta d'auke da siriruwar salla. wani sasanyan kamshi ne yabi hancinta. ta shaki iskar tare da lumshe idanunta a lokaci guda ta bud'e. Ido ta shiga rarrabawa cikin had'ad'd'e kuma rantsastsen parlour'n da tsaruwar sa ya kai tsaruwa. can ta hango sa kwance da baya saman doguwar kujera, ya yi pillow da hannayen sa, idanunsa a kan TV. a sannu tashiga d'aga kafafun tana takowa cikin parlour. sanyi da kamshi suna dukan ilahirin jikin ta, har sikar jikin na na tashi. yana kwance bai motsaba tamkar bai san da shihowar mutum parlour'n ba. Ta karaso ta tsaya d'an nesa da shi, cikin siririyar muryarta mai fita da yanayi shagwab'a ta ce "Wai gashi inji Ammie na." kamar bazai motsa ba bare ya yi magana, tsawon mintuna biyar tana tsaye, bai kalli in da take ba. zuwa can ya zare hannunsa guda da yayi pillow da shi, ya yi mata alama da ta miko masa. a sannu ta d'aga kafarta ta maso inda yake. a hankali ta kai hannunta d'aya dake rike da ganyen nan ta had'a shi da jikin Mug d'in, ya zamana da ta rike Mug d'in da duka hannayen ta, kana ta miko masa. Bai rike ba sai zaro d'aya hannunsa da yayi, ya rike Mug d'in da d'aya hannun d'ayan kuma bazato taji ya cafko hannunta mai rike da ganyen. wani irin waro ido tayi, kirjinta ya buga rass, ya aje tea'n saman table d'in gabansa, batayi aune ba taji ya fisgota, ta fad'o kansa. wani irin d'auke numfashi tayi tare da sakin kara. hannunta mai ganyen ya kama ya dad'a dunkule shi ya matse da karfi. kara ta kuma sakewa tana jujjuya fuskarta cikin kirjinsa, jikin ta na b'ari. ya saki hannun nata tare da ware tafin hannun, ganyen da yake kore ya dawo jajazir, ya ciro shi cikin hannunta ya cusashi ta d'an bakin rigarta ta saman kafad'ar ta kana ya ture ta a jikin sa, ta fad'i tim a kasa. da sauri ta mike tana wiki-wiki da ido, tare da yarfe hannunta da take jin sa kamar ba nata ba. ta waiga gefe da gefen ta wayam babu su Chuchu da sukace zasuzo su taimake ta. ya mai da hannayen sa ya dad'a yin pillow da su, yana aika mata dugun kallo. baya ta shiga yi kana da sauri ta juya cikin sassarfa tana fita daga parlour'n ta jingina jikin garo tana mai da numfashin tsoro. Sai kuma da sauri ta nufi get har tana had'awa da sassarfa. a in da ta bar su Chuchu a nan ta same su. fuska ta kwab'e kamar zatayi kuka. "Ya dai Feeryal kin sa masa kuwa?." suka had'a baki wajen tambayar ta. narai-narai tayi da ido sai ga guntun hawaye ta d'ago hannunta daya matse shi tana jin sa kamar zai fita, ta ciro ganyen a hannun rigarta ta gefen kafad'ar ta. da sauri Chulu ta karb'a tana fad'in "Ya tabbata ke nan shugaba ya yi gaskiya koren yanye ya dawo ja." a tare suka saki murmushi ita da Chulu. cikin rashin fahimta take duban su suda zasu nuna damuwar su, ya b'ata musu shirin sai kuma taga suna murna. murya na rawa ta ce "Ya gani fa shine ya matse shi a cikin hannuna har sai da ya canza kala, kamar zai b'alla min hannu, shine ina baku zo ba." Chuchu ta ce "Wayo yake da shi ya yi saurin ankare wa ne da akwai abu a hannunki duk da baisan mene ne ba, sai dai daya karanci idanun ki yaga d'aukar fansa cikin sa, shi yasa ya miki haka, amma kar ki damu shike nan yanzu dai tun da haka ne ya gane sai a canza tsari." baki ta cuno ta ce "Aa ni dai bazan sake ba karya min hannu zaiyi, ni na barshi da Allah mugu kawai." Har bakin kofar parlour'n Aunty suka rakata ita ta shiga, su suka juya domin isar da sakon da suka gani. Washegari ta karance ranar juma'a Dubbanin d'arurruwan jama'a ne suka shaida d'aurin auren Abdurrahim da amaryar sa Kuraiba. auren da ya had'a al'umma daban-daban na kasar nan da ma wajen kasar nan. biki ya yi biki duk wan da ya ziyarci gidajen bikin nan sai ya jinjina irin bajindar da ake zubawa. musamman gidan A.A FIYA. nera takoka a wannan ranar. Gaggarumin liyafa Mommy ta had'a a babban filin taro da ke cikin birnin Lagos, inda ta gayyaci manya-manyan mawaka dan su kwankwaje basirar su dan nuna farincikin wannan aure. da misalin karfe 8 na dare za'a fara gudanar da shagalin, in da za aje a d'auko amarya awuce da ita can gurin liyafar, idan aka gama gudanar da shagalin bikin a garzayo da ita gidan angonta. 'Yan uwa da abokan arziki anata shiri domin halartar filin taron. su Mommy anata shiga da fita na kayayyaki masu tsadar gaske. ko yanzu ma wani dokakken leshin da akayi mata odan sa daga can ketare ta saka, wan da dashi zata fantama a filin taron. Umma Karima da kyar ta iya danne damuwar ta ta fito cikin mutane tana dariyar yake, itama ta saka kaya masu tsada, duk da kasan ranta bakin cikin zuwan wannan ranar take. amma tayi imani da abin da bokan ta ya fad'a mata. haka ta tausasa Siyama da kamar zatayi hauka sabar kishi, ta yi wanka ta fito. Aunty ma tayi kwalliyar ta sosai duk wanda yagani sai ya yaba. Tun da yamma masu kwalli da aka gayyace su suka zo. suna ta cab'awa kannen ango kwalliya, zuwa magriba kannen ango sun fita ras, kamar wanda za'aje gasar kyau. ana isha'i motoci suka fara jidan mutane zuwa filin taro. su Hajiyan Dubai da wasu 'yan'uwan su Daddy da suka zo daga Yelwan Shendam akayi da su gidan amarya idan suka d'auko ta su wuce da ita filin taron. Dr Imran ne tsaye a kan sa, yana ta fama da shi ya tashi ya shirya su tafi, antafi d'aukar amarya bai kamata ace amarya ta isa su basu isa ba, su yakamata su jira zuwan amarya. ya ce bazaije ba idan yana da karfi yajashi ya kaishi. ganin da gaske ba zaije ba, yafita yaje sashin Mommy ya sanar mata. Mommy sun fito da kawayen ta zasu tafi, Imran yake sanar mata da abun da ya ke faruwa. da kanta taje ta same shi, ta ce har idan ita ta haife shi to ya tashi ya shirya, tun bai had'u da mummunar b'acin ranta ba, ita da tayi zaton ma har ya tafi yana tare da amaryar sa. badun yaso ba ya tashi ya shirya cikin wasu kaya masu shegen kyau. suka fito suka nufi filin taron da sauran abokan sa. Ko da Miemie ta zo suje da Feeryal ai mata kwalliya, Aunty ta ce ita bazataje gurin bikin ba, su tafi kawai. Miemie kamar zatayi kuka tayi ta had'a Aunty Allah da annabi. suna cikin haka Daddy ya shigo ya ce su tafi. Miemie murna har da dariya ta janyo Feeryal zuwa sashin Ammah bayan ta kira me kwalliya can. Miemie sai mita take mata "Ke wlh Feeryal gaba d'ayan ki sai a hankali, ki duba kiga kowa ya yi kwalli tun d'azu nake ta kiran ki kizo amiki kikaki zuwa, gashi har an fara tafi su Ameerah duk sun tafi, da nima fa na tafi jiran ki nake tayi tun d'azu, haba dan Allah." "Ke Ammie na ne fa ta ce bazan je ba, dama ni ma ba wani son zuwa nake ba, ni wlh dama yanzu nayi bacci na, tun da ina off ba salla zanyi ba me zan zauna yi." hararar ta Miemie tayi, ta ce wa me kwalliyar tayi mata da sauri dan Allah. Simple makeup akayi mata a hakan ma da kyar ta tsaya dan cewa tayi ita bata so. mai kwalliyar ta ce ba laifin ta bane ita kanta kwalliya ce, bata bukatar karin kwalliya. ta saka ashoben ya zauna a jikin ta kamar dan ita aka halittasa ta d'aura mata d'ankwalin, tare da rataya mata wani d'an siririn gyale. kana ta bi jikin ta da turare. Miemie da mai yin kwalliyar duk tsayuwa sukayi suna karewa Feeryal kallo "Ya ilahi ya lillahi, zan iya rantsuwa tun da nake harkar yiwa mutane kwalliya ban tab'a yiwa wata kwalliya a 1time ta haska tamkar wacce na d'au Three hour ana mata kwalliyar ba, ba wani fenti nayi miki ba paudar ma sama-sama na goga, ba kwalliyar ce tayi miki kyauba ke ce kikayi wa kwalliyar kyau, sai kace ke ce amaryar." Miemie da ta bud'e baki sai yanzu ta rufe "Idan da amaryar ta sami kyanta ai da ta gode da bamusan in da rawan kanta zai tsaya ba, yanzu ma yaya, muje Feeryal nasan yanzu kam kowa ya watse ma saura mu." Direban Ammah da Miemie ta hanashi d'aukar kowa tace ya jira su ya kaisu, shi ya d'auke su zuwa filin taron........! Babu editing 14 Tun da suka doso gurun baka jin ko mai sai sautin tashin kid'a. motarsu na fakawa Miemie ta fito da sauri tana fad'in "Feeryal yi sauri ana kan yi ban da mu." ta zaga ta gefen da take ta ruko hannunta suka nufi cikin Hall d'in. Feeryal ta rike hannun Miemie gam ganin jama'ar gurin maza da mata gabad'aya ya tada mata hankali. "Miemie ni kam zan zauna a moto na jira ki idan an tashi ki zo mu tafi, ga mutane fa." "Dalla muje mutanen cinyeki zasuyi, illa iyaka ki zame musu abin kallo kamar dai yanzu da ido ya bar kan amarya ya dawo kan mu, ke ki natsu da'alla ki d'aga mana aji, saura ace azo ayi rawa kiki zuwa, zo muje ta can ga gurin zama." Da sauri ta d'ago ta hangi ango da amarya Kuraiba sai washe baki take, angon nata kuwa na zaune fuskarnan tafi ta kullum murtukewa da rashin annuri. "Ido ta waro ganin in da Miemie take nuna mata, sai sun tsaga ta sakiyar filin kafin suje gurin. "Miemie mu zauna ata can mana." "Ke tacan zamuje so nake a tantance kasa da sakuwa, sakanin kwalliyar mu danasu Ameerah, duba kika yadda suke kallon mu, kirika murmushin nan naki abin zai fi bada show, ki had'a da juya wannan idanun naki, kinayi kina irin wannan tafiyar naki kamar na yanga." Miemie ta karasa maganar da dariya.. itama dariyar tayi tana zame hannunta daga rukon da ta mata, ta zille tayi d'aya gefen. dole Miemie ta biyo ta. Biki ya yi biki mawaka ana ta gwangwaje basira kowa da kalar baje basirar sa da yake, anyi manni an zubda daloli. Feeryal sai zuba murmushi take abun ya burge ta ba kad'an ba. MC ya gayyaci ango da amarya da su fito fili. tun MC bai rufa baki ba Kuraiba ta mike, tana yi masa alama da ya taso. shiko fuska yadad'a had'ewa. da sauri Mommy ta mike daga gurin zamanta ta je ta ruko hannunsa, bakin ta yakasa rufuwa "Taso mana Abdurrahim yau fa ranar farinciki ne, taso ka rike amaryar ka ku shiga fili." badun kar ya dizga Mommy gaban kawayen ta ba, da babu abin da zai sa ya tashi, karfa-karfan da akayi masa ma na zuwa gurin ya ishe sa. ya mike ta kamo hannun amaryar ta had'a da nashi, ya zame hannunsa ya rike iya yatsarta d'aya. a haka suka shiga filin. wata sassanyar waka aka sakar musu, amarya ta takarkare ta rika tikar rawa, shiko yana tsaye abin ma haushi ya bashi ganin yadda ta dage take tikar rawa, sai kuma wani mammannewa take a jikin shi. Mommy da uwar amarya Hajiya Luba da Hajiyan Dubai da kawayen su suka taso, suka shiga b'arin kud'i a jikin su. sai kace ganye suke wasa musu. sai kirari ake musu, iyayen ango iyayen amarya. Farida ma ta taso ta bud'e bakin jakanta. Bayan su Mommy sun koma gurin zaman su, su Amerrah ma suka taso suka shiga wasa 'yan kud'ad'en da suka zo da su a jakarsu. Miemie ta mike tana fad'in ai na mance Daddy ya raba mana 50-50k ga naki ma a jakata." ta ciro d'aurin 'yan d'ari biyar-biyar sabbi tar mika mata d'aya. "Taso muje muyi masa liki." tayi maganar tana kokarin roko hannunta. da sauri yati baya da hannun ta tana cewa "Aa kyale ni je kiyi masa likin ga nawa ma duk ki had'a kiyi masa likin kawai." "Ai baki isa ba kowa ya je ya yi masa liki ke ce bazaki je ba, ai dai zaki je ki taya shi farinciki, Allah sai kin je taso muje." "Dan Miemie ni ki rabu da ni kije kiyi masa kawai ni bazani ba." Hannunta ta figa ta janyo ta tana tirjewa Miemie tana cewa fa sai ta je. d'an karamin bakin ta ta cuno tana bubbuga kafafunta a kasa tare da yarfe hannunta tana cewa "Ni dai Miemie ki barni ni dai bazan jeba." a haka ta janyo ta suka shige filin. wani irin tafi gurin ya kaure da shi ji kake rap-rap-rap. da sauri ta tsaida buga kafa da yarfe hannun da take ta d'ago kai da sauri. taga mawakin yana takowa in da suke ya yin da yake ci gaba da rera salon baitin sa, Camera ya dawo kan su. yana zuwa in da suke ya shiga ciro kud'i a aljuhun sa yana lika mata. aka kuma kaurewa da tafi had'e da hele.. kai ta sunkuyar a hankali ta soma yiwa ango da amarya liki kamar yanda taga Miemie take musu, amma kanta a sunkuye. sai shigowa filin ake madadin a yi wa amarya da ango liki sai mata liki ake. ita dai kanta a sunkuye bata yadda ta d'ago ba, tana ta lika musu kud'in hanun ta. "Kamar ke ce amaryar sai kike fi dacewa da angon." da sauri ta waiga bayan ta, wata babbar mace ce tsaye tana mata liki ta baya. murmushi matar ta sakar mata, itama tayi mata gajeren murmushi. tana juyo wa idanunta ya yi karaf da nashi. wani mugun kallo ya wurga mata, da sauri ta zame jiki ta fice a filin ta koma gurin zaman su. Amarya Kuraiba ta bita da ido. wace ce ita daga fitowar ta ta cinye taron ko ita amaryar ba a yi ihun fitowar ta haka ba. ta had'iye abu mai d'aci a wuyan ta, ta aje tambayar ta cikin ranta sai bayan biki zata bibiyi wace ce ita, da zata fito filin da aka tanadar domin ta har ta janyo hankalin mutane kanta. daga an ga 'yar wata kasa sai duk a rud'e. tayi kwafa a kasan ranta. ta maida hankalin ta kan angon nata, ta cigaba da shishigewa jikin sa. Daga in da Mommy ke zaune take ta aikawa Feeryal harara, wan da ita batama san tayi ba. Feeryal na zama ta sauke numfashi Allah ya gani ba son shi cikin irin wannan taron take ba. Bayan ango da amarya sun zauna aka gayyaci kannen ango. duk yadda Miemie taso ta tashi su shiga fili fir take, haka ta kyale ta ta je suka tika rawar su.. Duk da cikin taro ne bai hanashi busa sigarin sa ba, yana yi yana karkata baki irin na 'yan iska. cikin muryar 'yan kwaya ya ce "Kai dubi wata had'ad'd'iya zazzafan kayan dad'i." "Ai tun d'azu na lura da irin had'iye yawon da kake akanta, kai fa Jazu ba karamin maye bane amma na mata." wani dariyar rashin mutunci ya ke ce da shi "Ke Zuly mata abin so ne, wancan yarinyar ta tara kayan dad'i a guraren nan." dariya tayi tana kallon in da take "Ba karya kam ta aje komai zam-zam amma nan gani nan bari, sakanin ka da shi kallo daga nesa." "In dai zaki taimaka min me zai hana bazan samu ba." "Nawa zaka biya?." "500k." "Seriously yanzu nake son jin su a banki na." "Idan kika gama aikin ki zaki jisu, kin san dai bama haka da ke." "Baka da matsala." ta fad'a tana mike wa, ta nufi in da su Feeryal suke zaune. Kujerar da ke fuskantar Feeryal ta ja ta zauna da murmushi kan fuskarta tana fad'in "Sannun ku dai sister's to ya bikin?." "Gashi ana kan yi." cewar Miemie." zama budurwar mai suna Zuly ta gyara idanunta a kan Feeryal ta ce "Tun daga can na ke ta hango ki, na ce yau daren nan tawa ce nayi samuwar kawa, sunana Zuly." ta karashe maganar da miko mata hannu. ido Feeryal ta bita da shi batare da ta miko nata hanun ba, sai murmushin da tayi mata. Zuly ta dubi Miemie ta marairaice murya. "Kawar tamu bata magana ne dan Allah kice ta ce min wani abu mana." Miemie ta tab'e baki "Da alama dai yanzu ta kurmance." "Hahaha amma anyi kyakkyar kurma anan to a haka nake son ki da kawa, kin ga ke ma kin zama kawata tun da ke kawar kawata ce, ni suna na Zuly ke fa." maganar ta bawa Feeryal dariya. tad'an dare. Hannu Miemie ta mika mata kamar yadda itama ta mata tana cewa "Ni kuma Miemie ita kuma Feeryal." "Wow nice names, amma ku kannen ango ne ko naganku da ankon kannen ango?." Miemie ta ce "Eh mu kannen sa ne." sosai ta dage tayi ta zuba musu hira, Miemie uwar 'yan surutu tana taya ta. har Feeryal tad'an saki jiki tana d'an sa baki cikin hirar. Karfe 12 dai-dai aka tashi, motoci suka soma jidar mutane suna maida su gida. tuni ango ya shige nashi motar ya yi gida batare da yajira komai ba, dan dama ya yi yinkurin tafiya har sau biyu Mommy ce ke hanashi. aka kwashi amarya da kawayen ta aka tafi da su A.A FIYA STREET. Su Miemie sukayi waje gurin nasu motar. har gurin motar Zuly ta biyo su, suna kokarin shiga mota, ta ce "Dan Allah ku d'an jira ni na duba na gani ko motar da nazo ciki ta tafi, dama kai amarya zanyi sai na biku kawai." ta juya da sauri suna tsaye suna jiran ta jikin mota. Can ta nufa in da mutane suke tsastsaye da ala ma jiran mota suke. da sauri ta karaso gurin ta ce "Sannun ku mota kuke jira?." suka ce Eh. ta ce "Ga mota can babu kowa cikin ta, ku karasa mana ku shiga." ai ko da sauri suka nufi in da ta nuna musu, ita kuma ta yi saurin isa gurin abokin harkallar ta sukayi magana kana ta juyo da sauri, gurin su Miemie. mutanen da ta ce misu ga mota can suna zuwa kuwa suka kama d'uruwa cikin mota. Miemie ta ce "Aa ya ya haka ya da shiga mana mota?." suka ce gidan amarya zasu kuma ance musu wannan motar gidan amarya ce. Feeryal ta ce "Miemie rabu da su su shiga kamar zai d'au ke mu ai motar." tun kan ta rufa baki suka shige. Miemie ta shiga gaba tana cewa "To ai sai ki zo ki shiga nan mu had'u mu makuru." tayi maganar tana hura hanci. murmushi Feeryal tayi ta shiga ta zauna gefen ta tana kokarin rufe murfin motar, Zuly ta karaso gurin tayi saurin rike murfin "Ah me zan gani haka wariyar launin fata za'a gwada min, mota ta cika ni ina kasa, to ai kuwa sai dai ke ki fito, mu nima wata motar, yauwa gama mota can sauko dan Allah muje mu shiga can, ba girman ku bane zama a matse alhalin daga gidan A.A FIYA kuka fito, yaho muje can motar." ta janyo hannun Feeryal ta fito ta maida marfin ta rufa tana fad'in "Allah ya tsare gamu a bayan ku muma sai mun iso." direba ya ja motar suka fice daga harabar Hall d'in. "Muje ko ga motar can." suka jera zuwa gurin motar. ta bud'e gidan baya, maza biyu ne a zaune a ciki sai kuma d'aya a mazaunin direba, ta shiga ta masa can ta mannu da mazan sosai, ta ce "Shigo mu lallab'a, ko kuma kai fita kar mu tseta sosai." wan da yake jikin kofar ta can ya sauka ya koma gefen mai zaman banza. kana Feeryal ta shiga jiki a d'an sanyaye dan bata tab'a shiga mota da maza irin haka ba. Babu wan da ya yi magana a cikin su har suka fice. sunyi tafiyar da baifi na mintuna biyar ba motar ta tsaya. na mijin da ke gefen Zuly ya bud'e motar ya fita, itama ta sauka, shi ya dawo cikin motar ya rufe kofar. ta zago ta gefen da Feeryal ta ke ta d'aga mata hannu "Bye bye 'yanmata sai mun sake had'uwa." da sauri Feeryal ta dube ta cikin rashin fahimta. ita ko ta juya tana cigaba da d'aga mata hanu, ta shige wani motar da yanzu ya karaso gurin. tana shiga aka figi motar da gudu. wani irin juyowa tayi jin an......! 15 An wani rungumo ta, ido ta waro cike da matukar tsoro. ya dad'a wani cacumo ta yana fa d'in "Wayyo kai kaji jiki kamar auduga, ja motar nan da sauri mu karasa ko mai zai iya faruwa a nan, nazo har wuya fa." ya ja motar suka shari wata kwana, tuni cikin ta ya d'ura ruwa sai musu-musu take tana tutture shi. ta fashe da kuka da ihun niman taimako. a bakin get d'in wani hotel suka yi hon, a ka bud'e suka shige ciki. d'aya na mijin da ke zaune a gaban mota ya miko masa key dai-dai san da suka gyara parking. ya ce "Room 13 shine d'akin ku asha dad'i lafiya oga." wani dariya ya sake hahaha. yana shafa fuskar Feeryal da yayi dama-dama da hawaye. "Yi shiru mana zazzafa wannan irin kuka haka sai kace yanka ki zanyi, kayan dad'i kawai zan baki, kuma ke zake fad'i farashin ki da kanki, ba kyauta zan more kayan alatun nan ba, muje ki fad'i nawa zan biya." ya bud'e motar ya fito kana ya miko mata hannu ya ce "Zo muje ko 'yammata." da sauri ta matsa baya tana girgiza kai, hawaye na zuba. ya mika hanu ya janyo ta ya fito da ita tana tirjewa, had'e da ihu. Babu kowa harabar hotel d'in guri ya yi shiru, sai masu gadin hotel d'in su biyu. ihu sosai take tana fad'in a taimake ta. amma masu gadin sai dariya suke suna fad'in "Kai Zazuu kabi a hankali fa sabuwar hannu ce wannan da gani." ganin zata bashi matsal sai kawai ya ciccib'e ta ya yi ciki da ita. a bakin kofar room 13 ya direta ya rike ta gam da d'aya hannun sa, d'ayan kuma ya zura key'n ya bud'e kofar kana ya tura ta ciki shima ya shige ya zare key'n ya maida shi ta ciki ya kulle kofar. Sosai Feeryal ke kuka kamar zata shid'e, ta shiga magiya da rokon sa "Dan Allah kayi hakuri kar kayi min komai, wlh ni bana son kud'in ka bana so dan Allah dan Allah." ta kuma rushewa da kuka sosai. Shiko wani irin murmushi yake sakewa yana tako wa in da take, baya ta shiga ja tana girgiza kai. har ta garu da jikin gado, hankad'a ta ya yi a kan gadon ya hayo kanta, yashiga shafa gefen fuskarta "Oh zazzafa ki natsu mana, ni fa ba d'an yankan kai bane, ni kawai mai bada gudumawa ne agaggauce; baki tab'a sanin dad'in abin bane, ko kin hange sa a wando ne ya tsorata ki, ki nutsu mu more juna gaskiya zan sha zaki kamar zuma, ta ina zamu fara ko kin bani zab'i." yana maganar yana tafiya da hannunsa jikin ta. Ido ta rumtse da karfi tana bige-bige da shure-shure, had'i da kururuwa, jikin ta na kyarma. "Ki dai na wannan ihun babu wan da zai jiki a nan, ko an ji ma babu mai zuwa taimakon ki, ke dai ki baje kawai mu more." ya mike a jikin ta tare da rungumota ya matseta a jikin sa ya zuge zip d'in rigarta yana kokarin yin kasa da rigar. kara ta kwalla ta yanka masa cizo a kafad'a. da sauri ya sake ta yana murza gurin. ta mike da gudu ta duro a gadon, ta isa bakin kofa tana kokarin murza ki, ya bita ya ruko ta. ya janyo ta ya kuma tura ta a kan gadon. ya bita yana kokuwan tub'e rigar jikin ta. jikin ta na b'ari tarika ture shi tana kuka kamar zata shid'e. ganin yana daf da cire mata riga, takuma takarkarewa ta yanka masa cizo a kunne. yana sakin ta ta mike aguje ta shige toilet ta danna kofa ta murza key tana haki. ta sulale kasa tare da kuma fashewa da kuka, tana toshe bakin ta... A b'angaren su Miemie kuwa, har sun d'au hanyar A.A FIYA STREET. d'aya daga cikin matan da suke cikin motar, ta ce da 'yan uwan ta "Gaskiya fa dare ya yi karfe 12 da wani abu, yaushe har muje gidan amarya mu kuma juyawa gida, dare zai mana sosai, gaskiya muwuce gida kawai in yaso gobe sai muje, dan Allah direba ka sauke mu ko a kan titin, Area-rod ne mu karasa kaga babu masu abin hawan ma." Miemie ta juya ta kalle ta ta ce "To ai muma dare zai mana yaushe har muje can." "Dan Allah kiyi hakuri baiwar Allah tun da motar gida ce zaku koma ai, yanzu mu idan aka sauke mu a nan babu abin hawan da zata kwashe mu, ki tai maka a sauke mu a can d'in. Miemie ta yi shiru tana jan kwafa a kasan ranta. direba ya juya akalar tafiyar ta su izuwa Area-rod. a bakin titi suka sauke su kafin su suka juyo gida. Ko da suka iso gida, duk motoci sun dawo har kowa ya shige b'angaren su. amarya tana side d'in angon ta a b'angare d'aya na cikin side d'in. a babban parking lot ya gyara fakin ta fito. ta nufi sashin su. tun daga nesa ta hango Abdurrahim tsaye cikin lambon gefen sashin hajiya. yana sanye da wando 3qtr da singilet, hannunsa d'aya ya zura cikin aljuhun wandon d'aya hannun nasa kuma yana rike da mug, yana d'an kurb'ar Coffee. a hankali ta karaso batayi sammanin zai tare ta ya tambaye ta ina ta fito ba dan yasan daga gun bikin sa suke, sai kuma ta ji akasin haka. "Ina kika tsaya sai yanzu kika dawo, ina sauran suke." da sauri ta ce "Wasu 'yan uwan amarya ne suka bi motar mu muka sauke su a unguwar su, su Ameerah kuma sun riga mu dawowa ma." "Kowa ya dawo ke kad'ai ce a waje?." kai ta gyad'a ta ce "Eh." kai ya jinjina tare da kai mug d'in bakin sa yad'an kurb'a. sannan ya juya a hankali. Har itama zata juya ta jiyo maganar Aunty. "Miemie har kun bani tsoro ina kuka tsaya ne, har sai yanzu kuka dawo, ina Feeryal d'in take?, kowa ya dawo gida ku kuna waje." Miemie ta ce "Feeryal kuma ai tun d'azu ta dawo motar su ma ya riga namu dawowa, dan mu sai da muka biya muka sauke mutane kafin muka juyo gida." "To ina ta shiga ke nan ban ganta ba, dan tun d'azu nake zaune a parlour ina zaman jiran dawowar ku, a wata motar ce ta dawo?." Miemie ta ce "A motar 'yan'uwan amarya, motar mu data cika ne wata 'yar'uwar amarya ta ce tazo su shiga motar, mun rigasu tashi kam amma nasan dole zasu rigamu isowa dan mu sai da mukaje Area-rod kafin muka juyo gida." da sauri Aunty ta juya tana fad'in "To ko tazo ta shige d'aki ne san da na tashi a parlor'n banga shigar ta ba. Abdurrahim ya tsaida tafiyar da yake a hankali wanda yake jin duk abin da suke fad'a. Miemie ta juya tana shirin bin bayan Aunty ya ce "Ke Miemie zo nan." da sauri ta zo inda yake. ya tsare ta da ido tare da fad'in "Ya akayi kun tafi tare ke kika dawo ke kad'ai, wace ce 'yar'uwar amaryar da ta biyo, dama ta santa ne?." da sauri ta girgiza kai "Aa bata santa ba a gun bikin muka had'u." "Baku santa ba ta biyo ta?." ya jefa mata tambayar yana dad'a tsare ta da ido. in'ina ta soma da tsoron kar ta karb'i tsarabar bulala ta ce "Am..im dama...dama muna zaune ne tazo gurin zaman mu ta ce tana son Feeryal da kawa, bayan antashi kuma mutane suka cika motar mu, shine ta ce Feeryal ta sauko ga mota can suje su shiga, itama nan gidan zatazo dama kawo amarya zasuyi." Ido ya tsare ta dashi da kyau kamar mai son karantar wani abu. "Uhum dama ku da wasu kuka je?." yakuma jefa mata tambayar. "Aa ni da ita kawai mukaje, mutanen da suka biyo motar mu kuma cewa sukayi motar da suka zo ciki ya tafi." Kai ya jinjina bai kuma cewa ko mai ba ya nufi side d'in sa ta kofar baya. ita kuma ta bi bayan Aunty da sauri. Bai jima da shiga ba ya fito rike da makullin mota. motar da ya dawo da ita d'azu ya aje ta a babban parking lot ya shige ya yi wa motar key masu gadi suka bud'e masa get ya fi. Karfe 1 da mintuna 30 ya isa Hall d'in da akayi shagalin bikin nasa. a wajen get ya faka motar kana ya fito ya yi yi knocking d'in get d'in. masu gadi suka bud'e karamar kofa. ganin shine suka ce ya shigo, hannu suka mika masa suna yi masa ban gajiyar biki. ba yabo ba fallasa ya amsa su. d'aya daga cikin su ya washe baki yana cewa "Ranka shidad'e ya muka gan ka a irin wannan lokacin ko amarya ce tayi mantuwa aka zo d'auka mata." tsayuwar sa ya gyara ya ce "No! kowa ya tafi an gama watsewa ko a kwai sauran mutane?." "Ai ranka shidad'e tun karfe 1 aka gama watsewa babu ko wa a nan." "Ina ma'aikatan CCTV camera na nan?." Suka nuna masa da hanu suna cewa gasu ta can. da d'an sauri ya nufi kofar da aka nuna masa. ya bubbuga kofar aka bud'e. mutane uku ne cikin office d'in zaune gaban computer. ya mika musu hannu yana cewa "I'm Dr Abdurrahim A.A FIYA." da sauri suma suka miko masa hannu suna fad'in "Ango mun gane ka ai daga ta cikin nan muke hango ka, muna taya ka murna." kai ya jinjina kasa ya ce "Yauwa d'aukar nan nake son gani a fito min da shi." "To an gama yellab'oi." Nan da nan suka kusa cikin na'urar suka soma zakulo duk abin da ya faru a gurin. tun daga soma decoration d'in gurin har zuwa san da aka tashi kowa ya watse. shiru ya yi idanunsa akan Computer, da alamun nazari yake cikin kwakwalwarsa sai kuma da sauri ya ce "D'an dawo da baya ka zuko nan." dai-dai in da ya hango budurwar da ta zo gurin su Feeryal d'in. ya kuma cewa a koma baya, daga in da ta taso daga gurin zaman ta. ido ya kurawa mutanen da take tare da su. da ganin su ba sai an fad'a ba b'ata garin samaruka ne, sosai ya maida hankalin sa kan wanda yake busa sigari yana yi wa yarinyar nuni da hanu, in da su Miemie suke. da sauri ya ce "Kunna mad'aukin magana, zuko muryar me yake gaya mata!." "Sir mad'aukin maganar gurin ya d'an sami masala ba'a jin magana ta gurin." tsayuwar sa ya gyara tare da kalmashe hannayen sa a kirji yana karantar lab'b'ansu tare da fassara kalmomin su cikin kwakwalwa da zuciyar sa. Zare hannayen sa ya yi a kirji tare da shafa sumar kansa san da yaga, ta iso gurin zaman su, a takaitaccen lokaci sun saki jiki da ita, har Feeryal tana yi mata murmushi. ya yi musu alama da hanu suyi gaba, dai-dai san da aka tashi har suka fito gurin mota, da in da budurwar ta tafi taje ta sami mutanen da tace suje su shiga motar su, sannan ta wuce gurin samarukan daga nan kuma ta kuma dawowa gurin motar ta fidda Feeryal daga cikin motar. suka shiga wata mota, da wad'an nan maza uku da suke tare da yarinyar. "Oh sheet!." ya furta tare da naushin iska. suma ma'aikatan jikin su ya yi sanyi sosai duk da basu san me ke faruwa ba amma sun fahimci shirine na kwamushe. "Sir kalli nan." suka fad'a suna nuna masa cikin computer. da sauri ya sauke idanunsa kan dai-dai in da budurwar ta sauka ta shige wata mota tana yiwa Feeryal bye bye, sukayi gaba. motar da Feeryal d'in take ciki shima yabi wata hanyar. Da sauri ya ce "Bi bayan motar ta ina sukayi!." "Daga nan ne camera'n mu dake wannan kusurwar ta tsaya." da sauri ya juya ya fita. masu gadi suna yi masa sai da safe, hannu kawai ya d'aga mu ya yi waje cikin hanzari ya shige motar sa... Feeryal na durkushe cikin toilet sai b'ari take da rusar kuka. shiko sai bubbuga kofar ya ke yana cewa idan bata bud'e ba idan ya b'alla kofar ya shigo sai ya yi mata kaca-kaca, ba shi kad'ai ba sai ya kira yaransa ma sun yi, daga nan su jefar da ita a titi. ganin zata bashi wuya ne har ta fara gajiyar da shi. ya zaro wayarsa ya daddanna ya kai kunne "Kuyi sauri ku shigo yarinyar nan zata bani matsala." yana fad'in haka ya sauke wayar. Kai ta girgiza murya na rawa kamar tana gaban sa cikin muryar kuka take fad'in "Ka dubi girman Allah karabu da ni, kar ka cutar da ni kaji tsoron Allah wayyo Ammie na, dan Allah kayi hakuri, ka barni na tafi kada ku cutar da ni, na rokeka dan Allah." ta kuma fashewa da kuka tana dad'a rab'ewa jikin murfin kofar toilet d'in. bata rufa baki ba mazan nan biyu suka shigo. ya ce "Ku b'alla kofar nan ku fito min da ita, ku baje min ita anan, idan na gama na baku ku karasa." Wani karfe suka d'auka suka rika dukan kofar da shi.. Wani kyakkyawan bugu sukayi wa kofar sai da ta b'alle. kara ta saka tana ja da baya cikin matukar tashin hankali. suka shige toilet d'in suka ciccib'o ta suka fito da ita. a kan gado suka wurgata. suka shiga jan kayan jikinta suna yagashi. wani irin kuka take kamar ranta zai fita. da sauri ya shiga tub'e kayan jikin sa yana fad'in "Wannan yarinyar akwai masifar taurin kai, duk yadda za'ayi ku tub'e min ita gaba d'aya ku baje min ita, na nuna mata taurin kai." Wani irin zabura waziri Kutup ya yi ya zube gaban sarki Matip, ya murza gashin bakin sa fuskar sa tayi tsananin baki sabar b'acin rai. "Tuba nake ya shugaba na, nakasa jure ganin halin da take ciki ne, ka gafarce ni akan maganar da zan kuma duk da ka hane ni, da zaka bani dama da na umurci runduna, mun cinmusu, ta firgita kwarai da gaske da lamarin su." Chuchu da Chulu da suke durkushe bisa gwuiwowin su, suna haki cikin sananin tafasar zuciya. suka ce "Ba sai an je da runduna ba mu d'in nan kad'ai zamu iya da su ko da sun kai runduna guda ne." sarki Matip ya girgiza kai yana cewa "Tabbaci da yakini kariyar da yafi namu yana gare sa, kafin tabbaci akan koren ganye izuwa ja, idan ya bari wani abu ya faru da ita to tabbas ya tabbata an sami rud'anin bincike, da kuwa ba zamu yafewa kanmu ba sai mun binciko shi a fad'in duniyar nan, ku da kanku kuka zo min da amsar koren ganye izuwa ja, ku d'ora yakini da tabbaci a kansa yana d'aure da nauyin da shi kansa bai san da shi a kansa ba, shi d'in garkuwa ne a gare ta." duk sukayi kasa da kawunan su suna d'aukar tabbaci... Da karfi yaja burki a dai-dai kwanar da yaga motar ta shiga ya kurawa hanyar ido, kana da karfi ya kuma figar motar ya kusa cikin layin. har ya yi nisa ya kuma juyowa ya rage gudun motar yana son tabbatar wa kansa rubutun da ke jikin sainbot d'in da ya wuce. Shanawa Hotel. sunan da ke rubuce a jikin sainbot d'in ke nan. da sauri ya kashe motar ya fito ya nufi get d'in ya shige cikin hanzari....! *Naso na baku yafi haka amma ban samu dama ba, sai kuyi maneji da shi, idan bacci bai d'auke ni ba zan iya kara muku abin da ya sauwaka zuwa da safe na baku, ba alkawari bane idan Allah ya nufe ni banyi bacci ba na ce zan yi* πŸ˜‚ 16 Da karfi ya tura kofar get d'in masu gadin suka mike, suna kokarin dakatar da shi. idanun sa ya sauka a kan lambar motar da a ka d'auke ta. cikin karaji ya ce "Ina suke ta ina sukayi masu wancan motar." yana maganar yana nufa gurin motar. masu gadin suka biyo shi suna cewa "Babu wan da sukazo a motar nan wannan motar kamma tun jiya take nan, ba'a fita da ita ko ina ba." a zafafe ya bud'e murfin motar tare da zaro wayar sa cikin aljuhu ya kunna torch d'in wayar, yana haska cikin motar. da sauri ya mika hanu ya janyo gyalenta da yagani kasan sit ya d'ago yana kare masa kallo. "An ce maka wannan motar tun jiya take nan, me kake nima cikin sa." wani irin juyawa ya yi tare da d'auke shi da wani irin gigitaccen marin da sai da ya yi tangad'i ya zube kasa. da sauri d'ayan ya ja baya jiki na rawa. cikin fusatacciyar murya mai had'e da tafasar zuciya ya ce "Idan kuka kuma da katar da ni sai na yanke harshenan ku!." Da sauri duk sukayi baya har da wan da yake kasa dafe da kuncin sa, da yake jin sa kamar jini na fita sabar azabar marin da ya sha. Da karfi ya juya yana taka kasa har ana jiyo sautin takun sa, dip-dip-dip!. yana dad'a damke gyalenta dake hannunsa ya shige cikin hotel d'in. Direct gurin ma'aikatan hotel d'in ya nufa masu kula da kyamarorin tsaro. ya ce su binciko masa list d'in wad'an da suke cikin hotel d'in da time d'in da kowa ya zo. ganin binciken nasu na yi masa nawa ya juya da sauri har yana had'awa da gudu-gudu, yana bin kofafin room d'in kasa yana kasa kunnen sa. sai da ya zaga kofofin kusan duka, ya d'aga kafa zai haura stairs, a hankali ya dawo da baya ya juya yana kallon wata kofa dake ta can gefe da stairs d'in. sai kuma da sauri ya isa kofar room d'in idanunsa a kasa yana kallon abin da ke yashe a kasa dai-dai bakin kofar. a hankali ya durkusa ya d'auko shi yana juyashi a hannunsa, ya yin da yashiga hasko yanda ya ganta a gun shagalin bikin su tabbas d'ankwalin ta ne wannan. bai dawo daga tunanin da yake ba yajiyo ihu cikin d'akin. Ido ya waro da karfi tare da sakin d'ankwali da gyalen hannunsa kasa. cikin tsananin tafasar zuciya ya yi wa kofar wani irin naushi d'aya a take ta b'alle. A razane suka sake ta tare da d'agowa suna duban kofar. Zazuu da ke kanta yana ta kokarin zare pant d'in ta, su kuma sun rirtike hannayenta sun bankare masa ita a haka ba tare da sun gama cire kayan jikin nata ba. da sauri ya mike a kanta yana kallonsa, sai kuma ya ce "Dalla ku bankare min ita kun tsaya kallon sa, idan nayi na gama sai kuyi ku bashi sauran da gani shima a hanu yake, jira ka more kayan dad'i kaima, bari na gama na baku sauran." ya koma yana kokarin bin jikin ta. Wani irin takowa ya yi tamkar walkiya mai tafiya kan iska. ya wani kai masa naushi a hanci tare da shako makogwaron sa, da sai da idanunsa suka firfito kamar zasu fad'o kasa. nan da nan jini yashi tsastsafowa a hancinsa gami da bakin sa. ya wani irin janyo shi ya had'a sa da jikin garu-bango. ji kake gomm! ya saki wani wahalellen kara. da gudu mutane biyun sukayiyo kansa, dukansu ya had'e su ya shako wuyan su, ya rika had'a su da jikin garu sai da ya yi musu jina-jina kafin ya sake su suka zube kasa suna numfarfashin azaba. yakuma bin su da naushi dukan su da ogan nasu dake zube kasa yana ganin guri na juya masa. rai b'ace ya ke fad'in "Ku ga kunan tantiran 'yan iska ko daga kan yau bazaku sake kokarin yi wa wata fyad'e ba." sai da yaga basa iya kyakkyawan motsi kafin ya kyale su, yana huci kamar kububuwa. Feeryal da kyar ta mike a galabaice ta rakub'e gefe tana kankame jikin ta da kare in da suka yayyaga kayan ta, da hannunta. tana jan shashshekar wahala. duk fuskanta ya yi ja tsabar kuka. jikin ta ya yi taya-taya duk in da suka karceta garin kokuwar tub'e ta duk ya yi ja, abin ka da farar mace. Boturan rigar jikin sa ya b'alle ya zaro rigar a jikin sa ya rage daga shi sai dingilet. ba tare da ya kalli inda take ba ya wurga mata rigar. hannu na rawa ta d'au ka idanunta a kansa. ya bata baya ya zaro wayarsa ya daddanna ya kara a kunnen sa. a hankali ta saka rigar kan kayan ta da yake a yayyage, bata saka boturan ba sai ta had'e shi ta rike da hannunta. wayar sa ce tayi kara ya yi picking call d'in ya kai wayar kunnen sa. "Room 13." ya fad'a tare da sauke wayar. ba'ayi minti uku ba wasu maza uku suka shigo. ya ce su kwashe su su tafi da su. suka d'ago su suka kad'aya keyar su sukayi waje da su suka turasu cikin mota sukayi gaba da su. Ya taka zuwa bakin kofar room d'in ya d'au d'ankwali da gyalen ta ya wurga mata su batare da ya juyo ba ya ce "Zaki cigaba da zama ne a gun?." da sauri ta sauko a gadon ta biyo bayan sa tana saka gyalen a kanta ta ruko d'ankwalin a hannu, ka farta ba takalmi, dan bata ma sann ta ina takalmin nata yake ba. suna isa bakin get d'in hotel d'in. ya bi masu gadin da mugun kallo tare da nuna musu yatsa yana girgiza shi alamun gargad'i. ai da sauri suka sunkuyar da kawunan su. Ya yi waje ta bisa da sauri. har in da ya faka motar sa, tsayuwa ya yi jikin motar yana waya. taja ta tsaya gefe jiki a sanyaye. wani uban ihu ta saka tayi tsalle ta matsa gefe tana yarfe hannu. da sauri ya sauke wayar tare da juyowa yana kallon ta. ta durkushe kasa ta rike kafarta tana fad'in "Wayyo kafata." torch in wayarsa ya kunna ya d'an tako gurin. wata katuwar bakar uwar kunama ya gani, a dai-dai in da ta d'aga kafar nata. ya sa kafa ya take ta da takalmin sa ya murkushe. kana ya juya ya shige mota. Feeryal na durkushe rike da kafarta da ta ke jin tsananin zafi gami da rad'ad'i da da zugi. nan da nan kafar ta had'a zufa shatin gurin da kunamar ya d'ane ta ya kunbura ya yi ja. Hon ya danna yana hango ta ta jikin miron motar. da kyar ta mike tana jan kafar ta yi kokarin bud'e murfin baya taji sa a rufe. ta dawo gaba ta bud'e ta shiga. tana zama ya figi motar. Sai shashshaka take ja da yarfe hannu. duk AC da ke cikin motar, bai hana gumi tsastsafo mata ba. ta kasa zama sai juyi take kan sit. shiko bai ko kalli in da take ba idanunsa a kan titi. sai da sukayi tafiya mai nisa kafin ya gyara fakin gefen titi. Ya mika hannu sit d'in baya ya d'auko jaka ya bud'e, kayayyakin aikin asibiti ne da yawa ciki. ya bincika ya zaro wasu allurai guda biyu, ya had'a su a Syringe d'aya kana ya d'an dube ta fuskarsa babu wasa "Gyara." ya fad'a a takaice. sautin kukan ta ta kara, gani allura a hannun sa. sai ta shiga girgiza kai murya na rawa take fad'in "Dan Allah kayi hakuri kar ka min." fuska yakuma gimtsewa ya ce "Idan baki natsu ba sai na caka miki shi a baki, gyara na ce." ai da sauri ta kai hannu ta toshe bakin ta, tana binshi da kallon tsoro hawaye na fita a idanunta. kai ya kawar da ga kallon da take masa. ya mika hanu yaja rigar sa da yake jikin ta gefe, kana ya d'an ruko gefen rigarta ta baya da zip d'in sa ke bud'e. b'ari ta soma tana shirin cire hannunta a bakin ta. "Idan baki tsaya ba irin su goma zan miki ta ko ina." fuskanta ta kifa jikin glass d'in kofar motar murya na rawa ta ce "Na tsaya Allah na tsaya." kara ta kwalla jin ya nitsa mata allurar ta saman pant d'in ta jikin ta na b'ari. ya zaro allurar yana jan gajeren tsaki. ya jefar da allurar gefen titi kana ya maida jakar baya, ya gyara zaman sa yaja motar sukayi gaba. Ta d'ago fuskarta daga jikin glass ya yi dama-dama da hawaye da zufa har da hajina. mintuna biyar baya ta shiga sauke numfashi da ajiyan zuciya a hankali. a sannu tarika jin zugin yana raguwa gumin da yake karyo mata ma ya daina. A bakin get d'in wani ramb'asheshen hotel ya yi hon aka bud'e yasa hancin motar ciki. yana gyara parking ya wurgo mata handkerchief kan kafarta. ta d'auka a hankali ta kai shi fuskarta, wani daddad'an kamshi ya bi hancinta ta share fuskarta. ya bud'e motar ya fita kana ya zaga gefen da take ya bud'e ya yi mata alama da ta sauka. a hankali ta zuro kafafunta da babu takalmi, ta fito ya mai da murfin ya rufe. kana ya juya ya yi gaba ba tare da ya mata magana ba. ganin haka tayi saurin bin bayan sa. suna shiga cikin had'ad'd'en hotel d'in aka mika masa key. ya amsa ya yi gaba takuma biyo sa da sauri, zuwa kofar da taga ya tsaya yana kokarin zura makullin ciki. yana bud'e wa ya matsa gefe ya yi mata alamar da ta shi. jiki a sanyaye ta shige, tana shiga ya janyo mata kofar, shi kuma ya juya. Da sauri ta waigo tana duban kofar ganin ya rufo shi ya juya. d'an nummafashi ta sauke hankali ta karasa ciki, ta zauna bakin lafiyayyen gadon room d'in da yake a gyare tsaf. sai rarraba ido take. Fitarsa da kamar minti 20 aka turo kofar, da sauri ta d'ago. shi ta gani rike da laida mai d'an girma a hannunsa, ta sunkiyar da kanta kasa tana wa 'yan yatsun ta. ya tako zuwa in da take, ya aje laidar a gefen ta kana ya juya yakuma fita yana mai janyo mata kofar. A hankali ta gyara zamanta ta janyo laidar ta bud'e. ganin kaya ne ciki, a sannu ta cicciro su. doguwar rigar abaya ne a cikin laidar sa, da takalmi mara tudu sosai cikin kwalinsa. sai pant da pat duk a laidodin su sai bra shima sabo guda d'aya, da underwear, sai turare. kai ta sunkuyar kamar wacce take gaban sa. ta kai mintuna biyar kafin ta iya mikewa ta d'au laidar ta shige toilet d'in room d'in. a gyare tsaf ko ina kwalkwal. ta aje laidar ta tub'e yagaggun kayan kijin ta. sai sannan taga in da jini ya b'ata bayan rigar. wani kunya ya kamata, sai mammakewa take kamar wanda ake ganin ta. da sauri ta d'ago rigar sa da ya bata ta rufe jikin ta, taga shi jinin bai tab'a ba. sassanyar numfashi ta sauke. da kyar ta karasa cire ragowar kayan jikin ta, bra da pant da pat d'in da ya karkace garin kokuwa har jini ya sami damar b'ata mata kaya. kana tayi wanka da sabon sabulun da tagani a toilet d'in cikin kwalinsa. Kana ta d'au pat da pant da underwear duk ta saka. ta d'au abayar ta saka batare da ta sa bra'n ba, dan dama ita ba ma'abociyar sa bra bace, na jikin ta ma dama yana ta damin ta. kana tayi mayafi da d'ankaalin abayan. sannan ta feshe jikin ta da dadad'an turaren, tana yi tana lullumshe idanunta dan ba karamin dad'in kamshi ya yi mata ba. duk kayan da ta cire ta had'a ta zuba su cikin dosbin da ta gani a cikin toilet d'in. kana ta fito da sauran pant da pat da bra'n da batasa d'in ba, da kuma rigar sa. a bakin gado ta zuba su tana zama akayi knocking jin shiru ba'a turo kofar ba ta ce a shigo. wata ma'aikaciyar hotel ne ta shigo sanye da uniform irin na ma'aikatan hotel. tana rike da katon tray ta karaso tayi mata sannu sannan ta dire tray'n saman table, ta fita. Ido ta zubawa tray'n kayan abincin yadda take jin kanta ma bata ko jin yunwa, burinta yanzu ta ganta kusa da Ammie'n ta. Ba'a jima ba ya shigo, ganin bata ci komai ba ya tab'e baki. ta mike da sauri gudun kada ya juya, gashi ya fi ta sauri bazaka fahimci saurin tafiyar sa ba sai idan kuna jerawa, har da sassarfa sai da ta had'a d'azu kafin ta cim masa. yadda ta miken ya baiwa jikin ta damar motsawa. karaf idanun sa ya sauka a kanta. da sauri ya janye idanunsa tare da sauke shi kan gadon "Wannan fa kin bar ma wa ko ma ki saka kafin ki fito." ya yi maganar tare da juyawa ya fita. a hankali tabi in da yake nunawa kan bra'n da bata sakaba. ta kuma maida idanunta kan kirjinta ido ta d'an waro ganin gyalen abayar bai rufe mata kirjin duka ba, ga kan ababen kirjin a tsaitsaye sunfi to sosai ana iya hango shatin kansu ta saman rigar. taji matukar kunya sosai jiki a sanyaye ta d'au bra'n sai da ta koma toilet kafin ta saka ta fito. ta kwashi sauran kayan ta zuba su cikin laida kana ta koma ta zauna. Ganin shiru bata fito ba ya turo kofar, tana ganin shi ta mike da sauri ta zura takalmin wan da ya yi mata dai-dai kamar an gwada ta,tabi bayan sa. Tun da suka shiga mota suka fara tafiya ko kyakkyar motsi batayi ba har suka iso gida. lokacin karfe 3 na dare.......! 17 Tun bayan wasewan 'yan kawo amarya amarya Kuraiba ta mike ta tub'e kayanta, ta fad'a bayi, ta kuma solle wanka, ta saka wasu kaya da babu marabansu da babu, dan komai na jikin ta a na gani. ta shafa turaruka ta d'au ko jakar kayan matan ta, ta sha na sha ta cusa na cusawa, sannan ta haye gado. tana zuba idon ganin angon nata, amma har d'aya tayi biyu ta wuce babu alamar sa. tayi sintiri cikin d'akin har ta gaji ta kwanta, bacci ya d'auke ta. Tashin hankalin da Aunty ta shiga ba zai misaltuba. Daddy yasa aka bincika gidan gaba d'aya babu ita. bai masa ba ya zaga da kansa, Mommy da Umma Karima suka rika mita, wai ya tada hankali akan wata da ita ba komai bace, wata kila ma tabi saurayi ne dama ta saba. Hajiya ko cewa tayi, yaje ya kwanta kar ya yadda ya tada hankalin sa har ciwon sa ya tashi a kanta, dan bata da asara ita Hajiyar ce da da asara. A daren Daddy ya baza jami'an tsaro. dan su tunanin su mai tawagar d'aukar amarya ne ya turo mutanen sa suka d'auke ta. a b'angaren Ammah ma ita da Miemie Abbie basuyi bacci ba, fargaba da tunanin halin da Feeryal d'in take ciki ya hanasu rumtsawa. Abbie da Ammah suka sako Miemie gaba da wayarta da sukayi hoto da yarinyar da suka tafi da Feeryal. sukaje sashin Aunty. Daddy ya ce a daren nan kuwa zai bada binciken yarinyar, duk suka d'ungumo sukayi waje. Abdurrahim na gyara parking Feeryal ta kai hannu tana kokarin bud'e motar maganar sa ta jiyo "Ina ke aljana ce me ya hana ki iya kare kanki?." da sauri ta waigo ya tsare ta da ido. yana nad'e bandaji a hannunsa, daya d'an ji rauni garin dukan su, yana d'an fidda jini. a hankali ta sunkiyar da kanta, ta bud'e kofar ta fita. ta na tsaye sai da yagama wayar da yake kafin ya fito, ya yi gaba ta bi bayan sa. gidan shiru babu motsin kowa sai security dake bakin get. da sauri ta d'aga kafa ta biyo shi da sassarfa jin kukan magen Hajiya da ga sashin ta. dai-dai san da su Daddy suke fitowa. ganin su tare cikin hanzari suka nufo su. Daddy yana fad'in "Abdurrahim tun d'azu da na neme ka security suka ce min ka fita, nayi ta kiran ka in sanar maka abun da ke faruwa baka d'aga ba, a ina ka samo ta." Daddy ya yi maganar dai-dai san da suke karasowa. Feeryal ta sa gudu ta rungume Aunty, tare da fashewa da kuka. Aunty ta rungume ta gam-gam tana fad'in "Feeryal ina kika shiga, nayi zaton wad'an can mutanen ne suka kuma d'auke ki, mene ne me ya same ki!?." Miemie ma ta rungume ta ta baya. baki ya tab'e ganin yadda take wani kukan shagwab'a. Ya cewa Daddy "Wayar da kake kira tana gida ne Daddy da d'aya wayar na fita." "Kai alhamdulillah duk hankalin mu ya tashi, mun d'auka mutanen nan ne suka kuma d'auke ta, amma dai babu wata matsala ko, a ina suka tsaya ne haka ko can gidan surukanka ne aka wuce da su? to kukan na mene ne kuma Feeryal ai mun godewa Allah tun da abin da muke zato bai faruba." kuma tab'e baki ya yi yana shirin barin gurin. Da sauri Daddy ya ce "Me ya same ka a hannu haka." kowa ya maida hankalin sa kan sa, Feeryal ta saki Aunty ta tsaya itama ta kallon sa, jiki a sanyaye dan tasan garin ceton ta ne yaji ciwon. "Ba wata matsala ba ce Daddy." ya fad'a a takaice Abbie ya ruko hannun nashi yana cewa "Kamar jini ne ke fita babu wata matsala kace?." "Eh ba komai Abbieh." ya fad'a yana wuce wa ya nufi side d'in sa. Feeryal tabi bayan sa da kallo murya a sanyaye ta ke fad'in "Ina ga garin dukan su ne yaji ciwo." da sauri kowa ya dawo da hankalin sa kanta. Daddy ya ce "Garin dukan su wa?." rau-rau tayi da ido sai ga hawaye sharr, murya na rawa take fad'in "Wasu ne wasu ne." sai kuma ta fashe da kuka. da sauri Aunty ta ruko ta hankali tashe sai yanzu ta lura da kayan jikinta wasu ne daban ba ashobin bikin sa ba. Aunty da hawaye ya fara zuba mata tashiga girgizata tana fad'in "Feeryal su waye ne niman gudu da ke sukayi, da niman yi miki fyad'e ko." kai ta shiga gyad'awa hawaye na zuba. Aunty ta kankame ta tana cewa "Allah bazai tab'a baiwa masu mugun nufi a kan ki dama ba, tun kina karamar ki ake bibiyar son ganin an ruguza darajar ki, Allah bazai basu sa'a ba." "Insha'allahu kuwa." cewar Ammah tana bubbuga kafad'ar ta. Jikin kowa ya yi sanyi Daddy yabi bayan Abdurrahim da kallo da yake shigewa side d'in sa. ya yi murmushi tare da girgiza kai "Abdurrahim ke nan da zurfin ciki wato baya son fad'a gudun kada hankali ya tashi." ya kuma girgiza kai, sannan ya ce kowa yaje ya kwanta ad'an tab'a bacci dan yanzu gari zai waye. Su Abbieh sukayi musu sai da safe suka wuce sashinsu. suma suka shige ciki. Daddy ya wuce bedroom d'in Aunty. in da Aunty ta ja Feeryal zuwa bedroom d'in ta, dan ta lura har yanzu akwai tsoro tare da ita ba lallai ne ta iya bacci ita kad'ai ba. kamar yadda bata saba b'oyewa Ammie'n nata komai ba ta labarta mata duk abin da ya faru a daren. Aunty ta ce sai an nemo yarinyar nan an hukuntata da bata da kishin jinsinta tana d'iya mace. Washegari a masallaci bayan an idar da sallah Daddy da Abbie suke tambayar Abdurrahim ya hanun nasa. ya ce ba ko mai ya warke. Daddy ya dube shi cikin kulawa ya ce "Jinyar jiya a ce yau ya warke." "Ba wata matsala ba ce da sauki Daddy." "Yauwa to dai da saukin zakace." Daddy ya fad'a ya juya yana amsa gaisuwar da ma'aikatan gidan suke yi masa. Dad daya zuba kunnuwan sa gurin su ya ce "Wai rauni yaji a hannun nasa ne?." Abbie ya ce "Eh jiya ke nan da aka nimi yarinyar nan Feeryal, ashe wasu 'yan iskan yara ne b'ata gari suka d'au ke ta, garin kwato ta ne yaji raunin." Dad ya kama baki yana cewa "Amma dai ba kariya ba dai ko?." Abbie ya ce "Aa haba ba kariya bane d'an jin ciwo ne kawai." "To Allah ya sauwaka." cewar Dad ya zame jiki ya yi cikin gida. Daddy da Abbie suka fito da Abdurrahim suna takowa cikin gida, Daddy ya dube shi yana cewa "Ya'yan su wane ne a garin nan, shin ka binciko iyayen su?." "Ban kai ga sanin iyayen su ba amma yau zan sani, dan suna hannuna." kai Daddy ya jinjina. Abbie ya ce "Ya kamata kam a binciko iyayen su dan sunyi rashin d'a a." Yana shiga side d'in sa ya wuce bathroom ya wasa ruwa kana ya fito ya haye gado. ba da jimawa ba bacci ya yi gaba da shi. A b'angaren Kuraiba kuwa, tayi mamakin har wayewan gari wajen karfe 10 batagan shi. batayi zaton abun da ya yi mata tana gidan su haka zai mata idan ta shigo gidan sa ba. tayi zaton zaiyi d'okin ta a matsinta na amarya da ko wani ango yake d'oki a daren farkon su. bayan tayi wanka tayi kwalliya ta fito, tana karewa kayataccen sashin nata kallo. kana ta nufi kofar da take tunanin wata kila ya kasance d'akin sa. tana tura kofar taga hanya ce ta bi hanyar ya kai ta har izuwa wani kayataccen parlour. a hankali ta nufi stairs tana takawa har ya kaita sama. nan ta kuma gamuwa da wata kayataccen parlour. ta tattab'a kofofin da ke cikin parlour'n taji su gam sai guda d'aya taji sa a bud'e ta tura ta shiga. Can ta hangosa kwance saman makeken lafiyayyen gadonsa yana baccin sa cikin kwanciyar hankali. ido ta kura masa tare da had'iye miyau, ta shiga takowa a hankali tana jin wani dad'i cikin ranta. komai da komai irin mikin da take mafarki. ta haye gadon ta fad'a jikin sa ta rungume shi tana wani dad'a shigewa jikin sa. tana shafashi tare da tura hanunta cikin rigar sa tana shafo kirjinsa. A hankali ya bud'e idanunsa, ya ture ta a jikin sa. da sauri ta kuma komawa jikin sa ta wani shagwab'e murya "Haba mijin Kuraiba jiya ina ka shiga ka barni ni kad'ai, da kyar nayi bacci ina ta jin tsoro." da sauri ya damke hannunta jin in da take kokarin tura hannun nata. ture ta a jikin sa ya dad'a yi tare da gimtse fuska, dan ya lura da yarinyar bata da kunya. ya mike ya shige bathroom. bayan sa tabi da kallo tana gyara kwanciyar ta a kan gadon. zuwa can yafito d'aure da towel da alama wanka ya yi. tana ganin shi ta mike taje ta rungumo shi. tana wani nannarkewa a jikin shi. "Haba mijin Kuraiba ban gane kana tureni a jikin ka ba, halaliya na ne fa, wai baka mararina ne." bai yi magana ba sai zame jikin sa da yayi yana kokarin matsawa gefe. takuma cakumo shi ta tura hannunta a........! 18 A kirjinshi tana shafo kan 'yan nonuwan shi, tana goga kirjinta a bayan shi. da karfi ya ruko ta ya juyo da ita, ya d'aga hanu zai yarfa mata mari sai kuma ya dunkule hannun. ya nuna mata kofa fuska ba wasa ya ce "Fita!. kallon sa tayi yana dad'a tsare gira, da nuna mata hanyar fita. kukan makirci ta sake tana fad'in "Korina kake." sai kuma ta juya da gudu tayi waje da kukan. tsaki yaja had'i da kwafa kana ya soma kimsawa. kiran Dr Imran ne ya shigo wayar sa yana gani bai d'aga ba. ya yi ta kira yana ji yacigaba da damuwarsa. sai da yagama kimsawa ya fito cikin shigar kananun kaya, sai baza kamshi yake. Dr Imran yana daga tsaye a farfajiyar bangaren nasa ne yake kiran sa. yana ganin fitowar sa ya nufi parking lot d'in sa, kamar baisan da shi a gurin ba, ya biyo bayan sa da sauri yana cewa "Wai haka ne dan mutum ya yi aure sai ya karo wulakanci, kana gani na ka wuce kuma tun d'azu nake kiran ka kaki d'agawa, kawai nayi maka uzini ne dan wata kila wani abun ne yake wakana a ciki, amma ka fito ka ganni sai ka share kayi gaba, wai ina ka kaisu ne kam, amma wad'an nan basu da mutunci ya akayi ne suka shigo gurin ma bayan akwai tsaro a gurin?." "Gidan gona." ya fad'a a takaice yana shige wa cikin d'aya daga cikin motocin sa. da sauri Dr Imran ya shiga d'aya gefen yana ci gaba da fad'in "Marasa mutunci da karya kasusuwansu kayi, ta in da gobe bazasu iya kuma bin wata yarinya ba." Wayarsa ce tayi kara dai-dai san da suke fita daga gidan ya d'aga, daga cikin wayar aka ce "Oga sun fad'i in da take." "Kuje ku d'auko ta." ya fad'a tare da kashe wayar. kana ya kara gudun motar. suka d'au hanyar fita daga gari. A b'angaren Kuraiba tana jin fitarsa, ta janyo wayarta ta kira number Mommy. da fara'a Mommy ta d'aga wayar tana cewa "Kuraiba antashi lafiya ya gajiyan hidima ya bakunta?." jin sheshshekan ta Mommy ta gyara zama tana kuma washe baki, abin nesa yazo kusa gani take jiya d'an nata ya angonce. "Aa mene ne na kukan Kuraiba ai hakuri zakiyi, sai kin daure kinyi jarumta." "Mommy jiyafa ko ganin sa banyi ba haka ya barni na kwana ni kad'ai inata jin tsoro, shine yau dan naje jikin sa ya kore ni yakuma fita a gidan, bansan ina yaje ba." murnar Mommy ya koma ciki wato abin da take zato dai ba shi ya faruba. ta ce "Kiyi hakuri bari na ne me shi." Mommy ta kashe wayar tana amsa sallamar da Mom tayi har ta zauna lokacin tana waya. ta ce "Yi hakuri ina waya kika shigo ban amsa sallamar ba." Mom ta ce "Ai dama yanzu 'yan gaisuwan biki zasuyi ta kira ana miki ban gaji." "Hm amaryar ce ma da kanta, ni bansan me ke damun Abdurrahim ba, wani irin murd'ad'd'en bahagon hali yake da shi, ki duba kigani jiya akai maka amarya kaje ka kwana wani guri ka barta ta kwana ita kad'ai gidan da bata saba ba, sannan ta taka taje in da kake ka kore ta, wani irin rayuwa ne wannan." Mom ta gyara zama tana cewa "Ina kuwa zai je gurin amarya yabi dare niman aljana, to ai in baki sani ba jiya kwana ya yi yana niman wancan aljanar yarinyar da ta bi wasu 'yan iskan samaruka, ya dawo gidan nan jina-jina sunyi masa kaca-kaca kamar har da kariya ko gocewar kashi a hannunsa, nace ina shi ina had'a tsafga da 'yan iska, yabar amarya a gida yatafi niman wata banza, d'azunnan Dad d'in su yashigo yake gaya min, ya ganshi a masallaci rab'e-rab'e Alhaji suna yi masa sannu da jiki." Mommy ta buga kirji "Iye kar ki gaya min wannna zancen ni ina ina ke nan akayi haka, au niman ta da jiya ake yi shine shi ya tashi ya bazama nima da sakan dare, kai wlh Allah ya'isa sakani na da Hajiya Fatima, ta gama da 'ya'yana maza ta gama asirce su kamar yadda tayi wa uban su." Mommy ta d'aga waya rai b'ace tashiga kiran wayar sa, sai dai ya yi ta ring bai d'aga ba. sai da tayi masa missed call wajen sau uku kafin ya d'aga. "Mommy ina driving ne idan na tsaya zan kira ki." d'ip ya kashe wayar. Mommy tayi ta bombomi uwar kawo gulmar Mom tana tayata. A bakin get d'in gidan gona ya yi hon aka bud'e masa get. ya na gyara parking ya fito Dr Imran ma yafito. da sauri wasu mutane biyu suka taho in da yake suna fad'in "Oga anje d'auko ta ba'a dawo daga d'auko ta ba tukun." kai ya jinjina tare da cewa "Ina suke, kun binciko iyayen sun?." ya yi tambayar yana tafiya ciki. suka biyo bayan sa suna fad'in "Suna ciki a kulle, asalin sunan sa Lukuman sunan gayun sa Zazuu shi d'an Alhaji Wali Dollars ne, su kuma sauran zaman kansu suke babu iyayen su a garin nan, sai dai tare suke da shi ko da yaushe." kai ya jinjina. Can cikin gidan gonar suka shige in da suka kulle su cikin wani d'aki mai duhu. suka bud'e mishi ya shiga. suka biyo bayan shi, wutan cikin gurin suka kunna tare da bud'e tagogi. gurin ya bada haske sosai. suna d'ad'd'aure, duk an tub'e su gajerun wanduna ne kawai a jikin su. sunyi mugun galabaita suka d'ago kawunan su, sai numfashin wahala suke saukewa. ya tako gaban su ya janyo kujera ya zauna. yana kare musu kallo. sai kuma ya mike yana cewa "Jaq miko min sandar can basu duku ba gaskiya." zabura suka yi suna cewa "Dan Allah kayi hakuri Yaya wlh mun duku, bazamu sake ba." murmushi Dr Imran ya yi sunji wuya har da kiran sa Yaya. Da sauri Jaq ya d'auko ya mika masa. sai da ya kewaye su da sanduna uku-uku duka rika ihu kafin ya jefar da sandar. kana ya sunkuya ya bud'e wata jakar da ya shigo da ita yana fad'in "Da alama bayi muku kaciya ba zo ku tub'e min su." Zazuu ya mirgina kai gefe cikin muryar galabaita ya ce "Wlh ammana ni tun ina jariri ma aka min." aska ya ciro yana gyara rikonsa ya matso gaban sa "Sabon kaciya zan maka idan ka warke zaka tantance, wata gona ya kamata ka rika shiga." yana gama fad'i ya cafko mazakutan sa da karfi ya murd'e. wani uban ihu ya sake jiki na kakkarwa. sai da ya tabbatar da ya azabtu kafin ya sake shi, ya kawo bakin sa saitin kunnen sa ya rad'a masa "Har yanzu bai kosa ba idan na kara ganin kabi wata sai na cire shi gaba d'aya." kai ya shiga gyad'awa a matukar tsorace zufa na karyo masa. Sauran suka birkice ganin ya d'ago yana kallon su. wad'an da suka kamo Zuly suka hankad'o ta ciki. suna cewa "Ga ta nan Oga mun kamo ta, sunan ta Zulaihat, inkiya Zuly 'yar Kano ce zaman kanta take a nan." ya juya yana binta da kallon kyama gami da tsana, wai mace ce wannan ta banzatar da kanta ta tsunduma harkar iskanci da shaye-shaye. ya tako gaban ta a zafafe yashiga d'auke ta da maruka da hannayen sa biyu ta ko wani gefen fuskarta. a gigice ta zube kasa sabo da wani irin masifaffen jiri sai take ji kamar ana jonata da wutan lantarki ne. Cikin fusatacciyar murya ya ce "Ku kamata ku d'aure ta kuyi mata aski." nan da nan suka rirtiketa sukayi mata d'aurin goro. Jaq ya aske mata kai tas har yana walkiya. ya janyo kujera ya zauna a gabanta ya kuma d'auketa da mari d'aya sai da gefen bakin ta ya fashe. cikin tafasar zuciya ya ce "Yanzu ke baki ji kunya ba, wai ke a hakan mace ce! sam baki dace da mace ba, da shashashshun maza irin wad'an can kika dace, shiyasa nasa a miki aski! da ke ake had'a baki ake cin zarafin 'yan'uwanki mata ke baki ji kunya ba!." ya karashe maganar tare da naushin kujerar da take kai a d'aure, tayi baya ta bugu da jikin garo. ya mike a fusace ya tako gaban ta cikin kakkausar murya ya ce "Kar ki sake na sake ganin ki a garin nan, ki koma gidan iyayenki ki samu miji kiyi aure, kina ji ko!!." ya karashi maganar cikin karaji sosai. ta zabura tana gyad'a kai ba kakkautawa, jiki na kyarma. Ya juya ya dubi su Jaq ya ce "Ku sake su, kuyi mata bukin Airplane ku bata 10 million yau d'in nan tabar ganin nan, kar ki sake nasake jin labarin ki a garin nan, su kuma a sasu a taxi zuwa gida." yana kaiwa nan ya juya Dr Imran yabi bayan sa. yana biye da shi yana ta kallon shi kamar bai tab'a sanin sa ba. shifa mamaki yake bashi baka tab'a gani alkiblarsa. har suka shiga mota suka bar gidan gonar bai fasa kallon sa ba. "Kai janye idanunka ka a kaina." ya yi maganar idanun sa a kan titi. "AA wai dama kasan ina kallon ka ne, nifa wallahi wani lokaci tsoro-tsoro kake bani, idan kayi wani abun sai naga kamar canzaka ake, sai na kasa gani wanne ne asalin wanne ne ake kawo shi jikin ka." hararar shi ya yi da wutsiyar ido yana cigaba da driving d'insa. Suna isa gida sashin Mommy ya nufa Dr Imran ya biyo shi. kasan cewar da ba'i a sashin nata ta kofar baya ya shiga, ya shige bedroom d'in nata. Mommy na zaune da wasu 'yan'uwan ta suna ganin shi suka mike suka fita bayan sun gama masa kirarin ango. Dr Imran ya zauna kan kujera yana gaisheta da yi mata ya gajin biki. tun kan ya zauna Mommy ta soma masifa "Wai me ke damun ka ne Abdurrahim, a kawo maka amarya jiya ka tsallaka cikin dare kafita kabar ta cikin d'aki, wai kaje niman wata mayyar aljana; ka barta ta kwana ita kad'ai a wannan makeken gida, tayi hakuri da haka ta aje alkunyar mu ta mata ta tashi da kanta taje in da kake ka zazzageta ka kore ta, kaki saurarar ta, anya Abdurrahim ka kiyayi fushina fa ka guji fushina akanka fa, na ce maka bakai ba aljanar yarinyar can babu wani taimako sakanin kai da ita, kai kasan wace ce ita kuwa yarinyar nan ba karamar hatsabibiya bace, ban yarda ba ban yarda kasake taimakon ta ba, ka barta ta tafi duk in da zataje, wad'an da sukayi lamanin ta suje su nemo ta; matarka kuma bana son sake jin makamancin haka, jiya da kyar tayi bacci saboda tsoro kar ka sake barinta ita kad'ai, akan wancan banzar yarinyar zaka sallaka kabar matarka cikin d'aki; kar na sake jin wannan nagaya maka ke nan." ya mike tare da nufar kofa yana cewa "Tun da tana tsoro, ta koma gida mana idan ta daina tsoron sai ta dawo." "Ai ko baka isa ba dan ba'a tab'a haka ba, kar ka sake ka wasa min kasa a ido ka sani shiga kunyar kawaye." Ganin ya yi waje Imran ya bisa da sauri cike da mamakin lamarin. suna fita waje Imran ya ce "Lallai wannan yarinyar 'yar sosai ce, auren jiya-jiya shine har an fara kai kara, karan ma akan miji bai saurare ki ba, to kai ma ka saurare ta mana me kake jira, da bazaka more angonci ba, kaje ka kwashi gara kawai mutumi na." wani kallo ya wurga mishi. Imran ya tsaya yana cewa "Ni bazan ma shiga ba daga nan zan tsaya, kai nifa tsoron yarinyar nan nakeji, kanaji Hajiya rannan ta ce da zakuna ta bisu, ga Mommy ma tana ce bakasan waye ita ba, to ni bari na koma daga nan, ban shirya had'uwa da damisai ba,bazanje ayi attack d'ina ba." Ya juya da sauri Abdurrahim yaja tsaki. Yana shiga bedroom d'in sa ya rage kayan jikin sa ya wuce bathroom. ya yi wanka ya fito, ya shirya cikin wando 3qtr da singilet. Kuraiba tanajin dawowan sa, tayi sauri-sauri ta shiga tayi wanka ta d'au wani yalolon riga iya cinya ta saka, sannan ta fesa turare. ta fito ta nufi b'angaren sa. tana shiga parlour'n sa dai-dai da yana sauka daga stairs kenan. tana wani taku cikin yauki ta karaso shima ya karasa sauka kenan, ta rungumo shi tana fad'in "Mijin Kuraiba tun d'azu nake jiranka, ina katafi ka barni, ga abinci can masu aiki sun kawo, yana wancan dinning d'in, yunwa nake ji nakasa iya cin komai bakanan, taho muje mu ci." zame jikin sa ya yi ya karasa parlour ya zauna. ta taho ta d'ale kan cinyarsa ta sakalo wuyansa, tare da kai bakin ta kan.......! 19 Kan bakin shi tana kokarin kissing lips d'in shi. ido ya ware kan fuskarta ya yi saurin kai hannun sa ya ture fuskar nata yana wasa mata wani kallo. shgwab'e murya tayi tana wani bankaro kirjinta da kusan rabin sa a waje suke ta ce "I'm sorry, I really love you shi yasa nake zuwa gare ka, You are very handsome, komai naka is so cute, ka daina kori na ajikin ka bazanje jikin wani ba, kai ne miji na, be with rne please. cikin side d'in can tsoro ya ke bani, ni fa ban saba zama ni kad'ai ba." tana maganar rana tafiya da hannunta daga wuyan sa zuwa kirjin sa." "It's okay tashi." ya fad'a yana kokarin ture ta. jikin shi ta shige ta manna nonuwan ta sosai a jikin shi tana wani dad'a narke wa. da karfi ya cirota tana kokarin kuma komawa jikin sa, ya d'auke ta da marin da sai da ta zube kan kujera, ya mike tsaye. ta saki jikin ta sharaf tare da ware kafafun ta. yadda ta zube ta ware kafafunta hatta pant d'in ta sai da ya bayyana ana hango shatin pussy d'in ta. cikin tsawa ya ce da ita "Stand up and get out! idan kika sake shigo min nan sai ranki ya b'aci, tashi na ce!." ta zabura ta mike ya kuma nuna mata hanya da hannu yana dad'a gimtse fuska. ba shiri ta bi hanyar. tsaki yaja ya d'au wayoyin sa yafita. Cikin garden yaje ya zauna ya d'au d'ya daga cikin wayoyin sa ya kira number Ajmal. Ajmal ya d'aga da sallama ya ce "Je ka karb'o min Breakfast gurin Aunty." Ajmal ya ce to. ya fito daga b'angaren su ya nufi b'angaren Aunty. Aunty na kichin tana shirin d'aura girkin rana, jin sallamar Ajmal ta fito. bayan ya gaishe ta ya sanar mata da sakon yayan nasu. Aunty ta isa dinning ta had'a masa nau'in abinci kala uku da Sudan tea daya fi so. tana mamakin har yanzu bai karya ba, tasan bazai tab'a cin abincin masu aiki ba in zai wuni, tun lokutan baya da Mommy tayi mata rashin mutunci akan samasa abincin da take, wai tana sa masa magani ciki duk ta mallake mata 'ya'ya mazanta, kar taje ta samusu guba suci su mutu. shari'a har gaban Hajiya. daga nan ta rage samasa abinci har yazo ma yabar kasar. daya dawonnan kuma idan ba shi ya aika ba bata sa a kai masa, gudun abin da zai je ya dawo sakanin ta da Mommy. Ajmal na tsaye idanun sa a kan kofar Feeryal. Aunty ta taho ta mika masa tray'n data shirya kayan breakfast d'in ya karb'a yana cewa "Aunty wai ina Feeryal tun da na shigo ban ganta ba." "Tana ciki tana bacci ne, bata jima da shiga ba tasha magani kanta na ciwo." "Subhanallah Allah ya sawaka." ya fita yana waigen kofar nata. Ya iso garden ya aje tray'n saman table d'in gabansa. yana shirin tafiya ya jiyo muryarsa yana fad'in "Me ya hanaka gyaran d'akin yau?." da sauri Ajmal ya dube shi, har yau d'in ma bai sami 'yanci daga bautar side d'in nasa ba, ai shi tun da akayi auren nan yake murnar zai huta da gyara masa side. bayan keyar sa ya sosa ya ce "Am Bro dama wai naga akwai babbar Aunty ce to nayi zaton zata had'a duk ta gyara." d'agowa ya yi ya dube shi. Ajmal ya shiga kame-kame. "To.to..tobari na je yanzu na gyara." ya juya da sauri ya nufi ciki. Ko da Ajmal ya gama ya fito lokacin yagama breakfast d'in ya kwashi kayakin ya mayarwa Aunty abinta. Kiran Mommy ne ya shigo wayarsa, yana d'agawa cikin fushi ta ce "Me Kuraiba ta maka zaka mare ta, 'yarka ce ita? kar na sake jin labarin ka kai hanu jikin ta idan ka kuma wlh ban yafe makaba Abdurrahim, kayi gaggawan zuwa ka bata hakuri idan ba so kake ka gamu da b'acin raina ba." "What! naje na bata hakuri fa kika ce Mommy." "Eh haka nace idan na isa da kai kaje ka rarrasheta, daga kawo maka mata zaka mai da ita jaka, ina dalili ina famari, so kake kasani a bakin duniya, a baka mata kana wulakantata, to wlh na gaya maka kar na sake ji, kuma umurni nake baka idan bakajeba ban yafe maka ba." Mommy ta kashe wayar tana cigaba da bombomi Teburin gaban sa ya nausa ransa ya b'aci matuka, ya mike rai a jagule ya shige ciki, da zummar d'aukar key'n mota ya bar gidan. ganin ta ya yi kwance a kan gadonsa, da wani rigar vest da wando iya cinya. tana jan sheshsheka. a zafafe ya nufo gadon ya fizgota zai yarfa mata mari. sai kuma ya dunkule hannunsa tuno da furucin Mommy a kan in ya kuma tab'ata. rungume shi tayi tare da sakin kukan makirci tana fad'in "Ko kashe ni zakayi bazan daina zuwa inda kake ba, dan bana son Allah ya kamaka akan hakkina na kulawa da ni." da karfi ya fizge jikin sa ya d'au makillin motarsa ya fice cikin fushi. bayan sa tabi da kallo tana wani lullumshe ido. Da daddare Kuraiba bata daddaraba ta yiyo d'akin sa wai ita a dole tsoro take ji. amma ko da ta tab'a kofar nasa taji sa gam haka ta hakura ta ja kafa ta koma. Washegari karfe goma tayi masa a AA FIYA Hospital. d'aya daga cikin asibitocinn sa da ke nan Lagos. ma'aikatan sa suka rika shan mamaki angon kwana biyu da zuwa aiki, wasu kuwa cewa suke wata kila CS ne ya kawo shi. Dr Imran ya shigo office d'in sa yana binsa da kallon mamaki. "Kai kuma me ya kawo ka, bayan mun baka hutun wata guda, kaje kaci amarci, Dr Omar, High Doctor of General Hospital, shima wata guda ya ce kayi, dan haka ka koma gida mu zamuji da sauran aikin, kar ma kace zaka wuce general hospital." hararar sa ya yi,kana ya mai da idanunsa kan system ya na cewa "What is the problem?." "Matsala ta ke nan ka tashi ka koma gun matar ka, ya za'ayi ma ka barta ita kad'ai ka fito." tab'e baki ya yi yacigaba da latsala system nasa. knocking akayi Dr Imran ya ce a shigo. ta turo kofar ta karaso ta tsaya gefe ta gaban sa ta d'an duka ta ce "Good morning sir." "Morning." ya fad'a batare da ya d'ago ba idanunsa akan system. "Am Sir akwai patient's masu son ganin ka, an aje su gefe ne bamusan zakazo yau ba, an tura files list d'in su a system naka, a sasu a layi ne?." "No! ba aiki nazo ba ku turasu gurin wani Dr." "Okay Sir." ta juya tana karairaya ta fita. Dr Imran yabi bayanta da kallo cikin muryar dariya ya ce "Yarinyar nan fa har yanzu da alama bata hakura ba, ga wani kallon da take maka." "Mttss." yaja dogon tsaki. jin surutun sa ya yi yawa ya ce ya tashi ya koma office d'in sa ya dame shi da surutu. Satin Kuraiba guda a gidan, yanzu ko daman ganin sa bata samu dan baya wuni a gidan, idan ya dawo da daddare kuma baya bata damar shigo masa dan yana dawowa zai rufe kofar sa. Da misalin karfe 7 na yamma motar Abdurrahim ne ya shigo gidan. akan idon Siyama har ya wuce side d'in shi. da sauri ta juya ta koma ciki, yanda ta fad'o parlour'n yasa Umma Karima cewa "Ke ya haka kamar an ingizo ki." sharaf ta zube a kujera, ganin sa yasata jin ina ma ace itace cikin side nashi yanzu zaije ya same ta. "Aunty Karima wai har sai yaushe ne aikin nan zai kammala, boka Mali dayace ana d'aura aure aiki zai fara baza'aje ko nan da can ba zan aure shi, amma har yau sati da auren sa babu wani alamun daya nuna hankalin sa ya karkata a kaina." Umma Karima ta sauke numfashi "Siyama nafiki shiga tashin hankali, sai dai na yadda da maganar boka Mali abin da na sani kawai bazai tab'a wasa min kasa a ido ba, mu dad'a jinkirtawa dai tukun amma gobe zanje naji me yake tafiya." Siyama ta karkad'a kai, gaba d'aya nutsuwa ya janye a jikin ta.. Kuraiba zaune gaban mirror tana jin shigowar motar sa ta mike ta leka ta jikin window. har ya gyara parking ya fito ya shige ciki, kafin ta saki labulen, tana juyowa wayarta ya fara ringing. ta karasa bakin gado ta zauna tad'aga wayar tana cewa "Besty ya akayi ne?." "Allah yasa dai ango baya kusa." "A'a baya kusa ya dai?." "Shi ke nan kinyi aure online d'in ma kin wasar gashi can munata tashin kan juna a group, wasu sabbin fitowa ne babu wanda bai yaba ba, ana tayi kina gefe, sabo da kina da mai sosa miki duk san da ya motsa miki, ki duba ki kara kwarewa, ki tashi kan ango da shi, ni dai yanzu nagama tashin kan cucumber na cinye." "Ai kuwa bari na duba yanzu." ta kashe wayar, tashiga Whatsapp. group nasu ne na kawayen su 'yan makaranta maza da mata, babu abin da suke sai ture-turen video batsa. shahararru daga cikin su kuwa sukan had'u dan kawar da sha'awarsu idan suka motsa sha'awar tasu a cikin group. tana shiga ta saki wani ihu ganin yadda ake zuba tsiya cikin group d'in. ai kuwa ana jin isowarta group ya birkice da sowa. ta bud'e blue films d'in ta soma kalla. nan da nan ta birkice. ta tura hannunta cikin pant d'in ta tashiga kwakular kanta. tana kallon yadda suke yi cikin video gaba d'aya ta rasa ina zata sa kanta. ta mike da saura ta tafi kichin tarika dube-dube tana niman inda zataga cucumber. ta wargaza kichin d'in tas bata gani ba. kai ta dafe, da a gidan su ne da ta samu ko nawa take so. dan sawa take a kawo shi sosai cikin kayan ganye, ita ta cusa musu ra'ayin cin cucumber sosai. Ta koma d'aki ta baje kan gado, tarika kwakular kanta da hannunta, wan da bata jin yana zuwa mata ko nan da can. wani irin mika tayi gaba d'aya jin kanta kamar kanta zai bud'e sabar yanda take jin kanta. a gigice ta mike tayi waje tana gyara d'aurin zanin da ke jikin ta. ta nufi d'akin sa kai tsaye. duk da bata da tabbacin samun kofar nashi a bod'e. tana tab'a kofar taji sa a bud'e wani numfashi ta sauke, ta tura ta shiga. tana shiga yana fitowa daga bathroom. fuska ya murtuke ya yi mata alama da hanu ta fita. da sauri ta tako gabanshi ta rungume shi tare da sakin kuka tana fad'in "Idan ka tauye min hakki Allah bazai barka, sati na guda a gidan nan baka tab'a taka cikin d'aki na ba, bakasan natshi lafiya ko akasin haka ba, haba mijin Kuraiba your partner must Satisfy your body and soul, me yasa me yasa kake son hanani zuwa gare ka, me I love you, ka gwada ni zaka fahimci ina son ka, son da nake maka yake sani aje kunya ta ta mace na zo gare ka, dan Allah ka daina korina ka barni narika zuwa jikin ka, inajin sassauci game da irin son da nake maka duk san da nake jikinka, ka barni na kwana da kai tsoro nake ji bazan iya kwana ni kad'ai ba." tana maganar tana wani irin shigewa jikin sa a haukace. tana yawo da hanunta a sassan jikin sa, ido ya rumtse lallai wannan yarinyar ba karamar shed'aniya ba ce, tana shirin kunce shi a matsayin sa na lafiyayyen na miji, dole yaji wani abu idan mace tazo masa a irin wannan tsigar. yana kokarin cireta a jikin sa ta saki zanin jikin ta ta had'e fatar jikin ta da nashi. ido ya kuma rumtsewa. ta yi baya ta janyo shi suka zube kan gado. jikinta na rawa. Ya yi matukar mamakin ganin yadda yarinyar ta kware a iya romance, sai da jikin sa ya yi sanyi da ita. baiyi sammanin wayewan nata yakai har haka ba. jikin sa bai dad'a sanyi ba sai da ya shige ta, duk da gyara da like-liken da gurin yaji bai hanashi fahimtar gurin a bud'e yake ba. Kuraiba kamar zatayi hauka gaba d'aya ta rikece ta gama susucewa, jin shi a jikin ta, lallai shi d'in bana wasa bane, girman dick d'in shi ya tsaya mata arai. tana jinsa fiye da yadda ta sammace shi. kukan makirci ta sake tana fad'in wai ya yi mata a hankali da zafi. 1h ya yi yaji gaba d'aya abin ya fita masa a kai, ya yi relax ya zare jikin sa ya yi bathroom. ya sarkake jikin sa ya fito ya ganta kwance shame-shame a kan gado, kafafunta a wawware. Fuska ba wasa ya ce "Tashi ki tafi." murya ta marairaice ta ce tana wani taune lips ita a dole zafi take ji, "Mijin Kuraiba please help me kaga in da gurin yayi kuwa, zafi sosai fa, gaba d'aya ka gajiyar dani bazan iya tashi." sawa ya buga mata ya ce ta tashi. ta mike tana kunkuni tajanyo zanin ta ta d'aura. tana wani tafiya a hankali ita adole zafi take ji. tayi waje. gajeren tsaki ya ja, ya saka kaya ya haye gado ya kwanta. Feeryal ce tafito daga bedroom d'in ta. Aunty na zaune a parlour ta karaso ta tana kokarin zama Aunty ta kura mata ido da sauri ta ce "Ina bra baki saba, koma kisa." baki ta cuno ta langwab'ar da kai "Ammie ban gani bane fa." "Bra'n ne baki gani?." kai ta gyad'a tana dad'a shagwab'e fuska. Aunty ta mike tana fad'in "Ni zan gani ai bari naje na nemo miki tun da sun b'ata." ta biyo ta tana bubbuga kafa kasa "Ammie duka wardrobe d'in fa babu." "Ai shine nace ni zan nimo, tun da sun b'ata miki ni zan samo su." tabi Ammie'n nata da sauri suka shige d'akin tana dariya da fad'in "Ammie numfashi fa yake hanani." "Ni dai a barni na nimo kawai tun da b'ata sukayi." cewar Aunty Aunty ta bud'e wardrobe ta rike baki tana kallon side d'in bra, tari guda har da sabbin da bata tab'a sawa ba. ta ciro mata d'aya ta ce "Gashi na samo miki daga in da suka b'atan, maza karb'a ki saka." ta na kokarin rufe wardrobe d'in ta hango laida, ta zaro shi tana cewa "Mene ne acikin nan ko har laida aka nemo na b'oye su ciki." ta yi maganar tana bud'e laidar ganin pant da pat da riga a ciki ta zaro rigar tana kare masa kallo. ido Feeryal ta waro ita sam tagama mancewa da rigar a gurin. tun ranar da suka dawo ta jefashi duka da laidar cikin wardrobe ta mance da shi. "Wannan rigar fa kamar ta maza ce ai wannan." cewar Aunty tana duban ta. "Laa namance na wannan ne daya bani a hotel d'in nan da suka yaga min kaya na saka." "Wai na Abdurrahim ke kamma Feeryal akwai shiririta, shine tun washegari baki mayar masa da kayan sa ba, to ai sai ki kai masa kayan sa kya aje a nan." ta mika mata rigar. "Kai masa yanzu ki dawo karb'i hijab ki saka." ta miko mata hijab ta karb'a ta saka. Aunty sai binta da kallo take tana murmushi, tayi kyau sosai cikin hijab d'in tamkar balarabiyar asali. Ido ta lumshe jin iskar waje ya bigeta. tun ranar da ya citota ya dawo da ita gida, bata kuma sa kafa cikin gidan ba sai ya. koda Miemie ta zo sunyi hira iyakar rakiyan ta da ita bakin kofar parlour. hango get d'in su Miemie tayi tana lissafin taje ta kirata ta rakata ta kaimasa. "Ko zai karb'a ma oho to amma ai jini bai tab'a masa rigaba ranar." tayi maganar ita kad'ai. ta sa kai tana shirin tafiya sashin su Miemie taji karar mota a bayan ta. da sauri ta waigo tare da matsawa gefe. motar tawuce. batasan wa ke ciki ba dan gilashin motar mai duhu ce. sai da ya wuce tasoma takawa a hankali. a gaban side d'in su Ajmal motar ta tsaya. Ajmal ya fito daga side d'in su ya zo jikin motar. tazo daf da motar ganin Ajmal a gurin ta juyo tana shirin gaida shi, idanunta ya sauka kan nacikin motar. idanunsa kan wasu files yana dubawa sannan ya mika wa Ajmal d'in. shi kuma ya karb'a yana yiwa Feeryal murmushi. itama ta maida masa a gajarce ya juya da sauri ya nufi parking lot yana gyara rikon files d'in. Ganin shine a motar tashiga takowa a hankali zuciyarta na tsalle, a sannu ta karaso jikin motar kanta a sunkuye. ta d'ago ta kalleshi, idanunsa na kan wayar da yake dannawa, tun ranar da ya taimake ta taji girmansa ya shinfid'u a ido da zuciyarta. a hankali ta miko masa rigar cikin siririyar muryarta ta ce "Nagode Sahab ga rigar." yakai 1min kafin ya d'ago idanunsa ya sauka cikin nata. "Sahab." sunan da ta kira shi da shi ya nanata a ransa. da sauri tayi kasa da kanta. shiko ya yi wa motar key ganin haka yasa ta d'an matsa gefe yaja motarsa ya wuce sashinsa. Kallon rigar tayi kana ta kalli bayan motar nashi, sai kuma ta juya. dan dama ta sammaci haka daga gareshi, tasan ba lallai ne ya karb'i rigar ba dama, ko ya yi sammanin da jini a jikin wannan rigar ne shima. rau-rau tayi da ido ta juya.....! 20 Tana daf da shiga side d'in Aunty tajiyo muryar Miemie tana kiranta. ta juyo ta tsaya tanata murmushi. Miemie ta karaso rike da yarinya a hannunta. "Ina kika fito ne Feeryal, shine kin fito ko nimata bakiyi ba ko." tab'e fuska tayi ta ce "Wannan Sahab d'in ne na kai masa rigarsa da ranar ya bani, yauma yaki amsa." "Ranar d'in ma jinin ya tab'a ne?." kai ta girgiza. "To ki ajiye idan kika kuma bashi bai karb'arb'a ba, sai ki bawa wani, um ga motar Ya Faruoq can mijin Aunty Farida, yazo zasu tafi bari na kai mata 'yarta, ko zaki rakani?." "Aa jike ina jiran ki anan." "Dalla zo muje ke zaman guri d'ayan ma ko damin ki baya yi, kullum kina nanike a ciki, ni ina zan iya ai sai dai in ciwo nake, shima ina jin dama-dama bazan zauna ba zanyi waje na mike kafa, d'an rike min ita na gyara." Feeryal na karb'ar ta ta ce "To muje." Miemie tayi sauri tayi gaba. Feeryal ta biyo ta tana fad'in "Miemie ki karb'e ta dan Allah." Miemie ta dad'a sauri tana dariya har suka karaso gurin motar Faruoq daya fito yana tsaye jikin motar. "Ya Farouq ina yini." cewar Miemie tana waigen Feeryal tana mata dariya. ya amsa idanunsa akan Feeryal data kwab'e fuska kamar zatayi kuka. hannu ya mika mata alamun ta miko masa 'yarsa da take ta tsallen ganin uban nata a hannunta. ta miko masa ita tare da gaishe shi. ya amsa idanunsa a kanta kana ya dubi Miemie ya ce "Miemie dariyar zolaya ko, me kikayi mata take b'ata rai." ta ce "Ni ban mata ko mai ba kwad'ayin kuka take ji, yanzu zakaga tana yi." tayi maganar cike da zolaya tana kallon ta. dariya ya yi yana cewa "Au haka take da saurin kuka, to gaskiya ya kamata a sami mai rarrashi, meye sunan kyakkyar?." Miemie ta ce "Feeryal sunan ta." kai ya jinjina yana cewa "Sunan dai-dai da yanayi." zai kuma magana Farida ta fito. wani irin daramm taji ganin Feeryal a gaban mijinta idanunsa tarr a kanta yana ta mata dariya. Miemie ta ce "Aunty Farida ai Neezrah ko kuka batayi ba tana ta wasan ta, zan zo har gida na d'auke ta muzo mu wuni." wani irin abu ta had'iye tamkar kayoyi a makoshinta, kai kawai ta iya gyad'awa Miemie ta bud'e mota ta shiga. Farouq ya ce "Anya kuwa Miemie ni dai a hannun Feeryal naga baby Neezrah ya tabbata dai ta iya raino ba ke ba." ya yi maganar yana bud'e gefen direba har lau yana yiwa Feeryal murmushi. Miemie ta bigi kafad'ar ta ganin tayi murmushi tace "Hum wai har taji dad'i sai kace ita tayi rainon." tafiya ta soma tana fad'in "Ai nima nayi daga can zuwa nan." Har suka fice a gidan Farida bata iya cewa komai ba tana zaune zuciyarta na tukuki. tun a hanya Farouq ya ke ta kawo mata maganarta ya na cewa yarinyar she is so cute completely. hirarsa d'aya biyu sai ya sakota, har duka isa gida bai fasa ba. suna shiga parlour'n su ta kwab'e mayafinta tana haki da yadda take jin zuciyarta kamar zai yi bindiga. Neezrah ya aje kan kujera yana fad'in "Zauna 'yar rainon Feeryal ko gobe zakije gidan su ne, dan naga ke ma sai murna kike a gidan su." cikin masifa da tafasar zuci ta ce "Badai gidan su ba sai dai gidan mu dan ba gidan uban Feeryal bane can." ta juya fuu ta shige d'aki. murmushi ya yi dan bai kawo komai a ransa ba ya cigaba da yiwa 'yar sa wasa. Da daddare har ya yi nisa a bacci ta tashe shi, dan ita takasa baccin, sabar masifar kishi. ta bubbugashi tana fad'in "Faruoq ta shi ka gaya min mene ne dalilin dayasa kake ta kawo min maganar mayyar aljanar yarinyar nan, tun a mota har a cikin gidan nan, wace munafurci kake kullawa cikin ranka." ido ya bud'e cike da bacci ya ce "Haba Farida a tsohon daren nan zaki tada ni da wani magana mara kan gado, babu ko Abba'n Neezrah ma yau to me zan gaya miki, me kuma zan b'oye miki cikin raina, dan nayi maganar kanwarki shine wani abun tashin hankali." "Dakata Faruoq ba kanwata ba karka sake had'a ni da ita, dan babu abun da ya had'ani da 'yar da ba'asan asalinta ba, tsintacciyar cikin ruwa, daga yau karka sake kawo min batun ta cikin gida har in kana son zaman lafiya a gidan nan." janyo ta ya yi jikin sa ya ce "To naji shike nan Sleep please bazan kara ba." Farida bata iya bacci ba sabar yadda take jin zuciyarta, kamar ana mata luguden tab'are. Washegari da safe bayan ya fita office ta shirya ta d'au mota sai AA FIYA STREET. tana isa b'angaren Mommy ta shige. Mommy na ganin ta ta ce "Ya akayi Farida ko jiya kinyi mantuwa ne?." ta ce "Nazo cin uwar mayyar yarinyar nan ne, jiya kwana Faruoq ya yi yana ambaton sunan ta, zo muje Sumayya ko Ameerah ku kira min ita." Ameerah tayi kus kamar bataji ba. Mommy ta ce "Ke Sumayya tashi kije ki kira mata ita, ai kiyi mata tatas in da gobe bazata kuma bin kurwar sa cikin dare ba." Farida ta juya ta fita Sumayya ta bita tana fad'in "Aunty Farida da kin rabu da ita." hararar ta tayi bata tsaya ba sai da tafito waje ta ce "Wuce kije ki kira min ita." Sumayya ta wuce sashin Aunty. a parlour ta tadda Aunty ta ce wai Farida tana kiran Feeryal. Aunty ta d'anyi jim sannan ta ce "Me ya faru ta ke niman ta?." ta ce "Ni ma ban sani ba tadai ce na kira ta." kai ta jinjina ta ce "Shiga tana ciki." Sumayya ta shiga ta sameta tana bacci ta tasota ta d'au hijabi suka fito. har sun kai kofa zasu fita Aunty ta ce "Tafad'i abin da zata fad'a ki dawo bance ki amsa ta ba." Feeryal ta gyad'a kai kana suka fita. Aunty ta koma ta zauna bataji ko d'arr ba dan tasan ba shegiyar da ta isa tasa mata hanu yanzu ta share, sai dai taji wa jikinta. Farida na ganin su tasoma tahowa tana fad'in "Yau nazo naci uwar ki har gida naga wanda ya tsaya miki." ta na isowa in da take ta shako wuyan hijabin ta. "Meye had'aki da mijina da zakisa ya koma gida yana kawo min zancen ki, maitar taki takai har kin fara bibiyar mijina, me za'ayi dake da ba a san asalinki ba, to wlh gargad'i na farko na karshe idan na sake ganin ki a inda mijina yake sai nayi miki d'anbanzan duka na b'ata fuskar da yake rud'in ki yake kaiki ga mazajen mutane, shegiya mayyar banza aljanar ruwa, nafi karfin ki wlh ba dai miji na ba." Ajmal dake tahowa ta bayansu ya ce "Meye haka Farida wani irin abu ne wannan meye amfanin hakan." cikin masifa fa ce "Karabu dani Ajmal naci uban yarinayr nan, dan wlh bata isa ba mijina yafi karfin ta." "Kaji wani shirme dan Allah ita cewa tayi tana son mijin naki." "Idan ta fad'a ma basai na kasheta ba, wlh mijina ya girmi ajinta 'yar da ba a san asalinta ba ma, idan bata fita sabgar miji na ba, wlh sai na halakata." kai Feeryal ta sunkuyar Ajmal na kokarin jan hannun Farida da ke rike da wuyan hijabin ta wayarsa tayi kara. ya zaro wayar a aljuhu ya kai sa kunne daga cikin wayar ya ce "Bawa Farida wayar." ya zaro a kunnen sa yamika mata yana cewa "Wai gashi." sai da ta harare sa kamar ita ce gaba da shi kafin ta ce "Inji wa nifa baza'a mareni a hanani kuka ba." ta fizge wayar ta kai kunnenta. Ajmal yashiga waige-waige yana son ganin daga ina yake har yasan abin da yake faruwa, yana d'aga kai ya hango sa can saman upstairs na side d'in sa yana tsaye rike da Mug a hannunsa ya yin da d'aya hannunsa ke kare da waya a kunnensa. daga cikin wayar Farida tajiyo muryar sa "Saketa! baki da hankali ne zaki rika d'agawa mutane murya a cikin gida, oya fita ki bar gidan nan ki koma gidan ki, kar ki kawo wa mutane haukar banza, kisa ta tarawa mutane jama'a." Farida ta tura baki ta mikawa Ajmal wayarsa. ta sake ta tana cewa "Allah ya taimake ki wlh da sai kin gane cewa mijina ba saranki bane, mayyar aljana kawai." ta juya fuu ta yi gurin motarta tashige tabar gidan. Ajmal ya dubi Feeryal da jikin ta ya yi sanyi yace "Yi hakuri Feeryal kije abin ki." a hankali ta juya. tana shiga Aunty ta bita da kallo ganin jikin ta a sanyaye ta ce "Me yasa Farida'r take niman ki?." murya a sanyaye ta ce "Wai nafita sabgar mijinta wai ya koma gida yana zance na." Aunty tayi murmushi tare da girgiza kai ta ce "Je kiyi wanka kizo kiyi breakfast." ta juya ta shige bedroom d'in ta. Ji ya yi an rungume shi ta baya, Kuraiba ta manna kanta a bayan shi tana shafa kirjinshi. cikin narke murya ta ce "Mijin Kuraiba ba ko zuwa duba ya na kwana ba, kasan da ya nayi bacci kuwa, gurin nan sai zafi yake min sai da nayita gasashi da ruwan zafi, ka duba min zafi yake min har yanzu." hannunta ya b'anb'are a kirjin sa ya juyo tare da wasa mata wani kallo kana ya juya ya bar gurin. wani uban mika ta sake tana tuna kasantuwarsu har yanzu zakinsa yaki gogewa a kwakwalwar ta, tana ji ina ma ace ta kasance cikin hakan yanzu.. Umma Karima ce tsaye cikin d'akin ta, rike da waya a kunnenta. daga cikin wayar ake fad'in "Hajiya sai yau Allah ya yi aka samo wani da kyar, in zaki biya million 2 idan guri ya rufa zan kawo miki." Umma Karima ta sauke wani nannauyar ajiyar zuciya tana fad'in "Allah na gode maka wahalata tazo karshe, million 3 zan baka shima ka rike ne dai-dai komai ya dai-dai ta zan biyaka kud'in aikin ka mai soka." "Hahaha Hajiya to na gode anjima zaki ganni." Umma Karima ta sauke wayar tashiga tika rawa. tana fad'in "Sai ni Hajiya Karima bani Dubai London bani England." tawani shekewa da dariya "Hahaha yanzu wasan zai soma.......! 21 Guri na rufawa kamar yadda mutumin da sukayi waya da Umma Karima yace zaizo kuwa sai gashi yazo. a parking lot d'in ta ya tsaya tafito ta sameshi. ya mika mata wata bakar laida yana fad'in "Ga sakon ki Hajiya na d'auki kasada sosai amma na shafe duk wata shaida." har hannunta na b'ari ta karb'i laidar tana cewa "Kai sannun ka da aiki kayi namijin kokari da kai za'aci arziki saboda kayi rawar gani wajen ganin an samo arzikin, yanzu ga wannan miliyan ukun ne, kaje ka sha shayi da su kayi murna lokacin arzikin ka yayi." ta mika masa jaka mai d'auke da kud'ad'en da ta shirya ciki. ya karb'a da murna yana fad'in "Lallai kuwa godiya nake Hajiya, ai muna fadarki muci arziki mu barta a inda take." har ya shiga motar sa bai fasa zuba mata godiya ba, yana fita tashiga kwad'awa Liti direban ta kira. ya shigo cikin hanzari yana amsa kiran nata. ta ce "D'auko makullin mota da sauri fita zamuyi yanzu." "Ina kuma zamuje Hajiya da magriban nan?." "D'auko da'alla a hanya kayi min wannan tambayar." ta shige mota da sauri tana rungume laidar da kyau a jiikinta. sai da suka haura titi kafin ya dubeta yana cewa "Hajiya ina muka dosa ko tafiya zamuyi ta yi kawai?." ta ce "Dajin Mali zamuje kara gudun motar yi sauri hanzarta." "Hajiya ba dai kud'i kika d'auka a laidar nan zaki kai masa ba, ni fa dama ina da bukatar wasu kud'ad'e sabo da na kwan biyu ban yi aike gida ba." "Ni matsala ta da kai ke nan, kullum baka da damuwa sai na kud'i, ko an baka sai ka kuma niman su, ka aje bukatar kud'in nan naka yanzu sai an gama komai tukun, Allah na tuba idan aiki ya kammala meye kud'i kuma ai sai dai ka bawa wasu, kai dai yi sauri mu isa." Liti ya kara gudun motar yana cewa "Wai gara in fad'a miki da wuri ne kar ki kwashi kud'ad'en duka ki kai masa mu mu rasa." Karfe 7 da rabi suka isa saboda gudun da motar take. Umma Karima ta sauko a motar guri ya rufa yayi duhu, babu tsoron Allah bare tsoron dukun dajin bare tsoron wani mugun dabba mai cutarwa. zuciyarta ya kekashe muradin ta kawai take hangowa a gabanta. ta kunna hasken wayarta ga kuma hasken fitilar mota. jiki na rawa na son cikan muradinta, sai kakabe laidar take a jikinta. ta cire mayafi ta kunce d'ankwali ta cire takalmi, ta d'uru cikin duhuwar kogonnan, zuciya a kekashe babu d'igon tsoro bare imani. "Gafara dai boka yau gani tafe da babban guzuri, nasamo cikon na uku." wani irin hargitsastsen dariya kogon ya kaure da shi "Hahahaha kinyi nazari da lissafi mai kyau, saura kiris laya ta gama narkewa jeki sanya shi cikin tukunya." da sauri ta isa gaban tukunyar kaskon tajefa laidar ciki. wani irin hargitsewa gurin ya yi da wani irin sauti mai ban tsoro, tukunyar ta kama tafasa tana dafuwa tamkar wutar zuga, wani kumfa ya taso fuuu yana bin jikin tukunyar yana gangara zuwa cikin wani rami mai zurfin gaske da ba'a iya hango karshen sa. jikin Umma Karima na rawa, idanunta a kan tukunyar, har kumfar tagama sauka tas tukunyar ta shafe kamar babu abinda ya tab'a zama cikin ta. kazamtacciyar dariyar nan ya kuma kecewa da shi yana fad'in "Aiki ya kammala ikon ki ya soma." zubewa gaban shi tayi tashiga karanto mishi ayoyin godiya. ya ce "Tashi kije gaki ga duniya kin samu." jiki na kyarma ta mike tafito daga kogon ta kwashi kayakin ta, tashige mota bakin ta yaki rufuwa. Liti ya kunna motar su ka soma fita daga dajin. ganin yanda yau ta fito cikin mashahuriyar farinci daga gurin bokan nata ya ce "Hajjaju an samo wata nasarar kenan." baki ta dad'a washewa ta ce "Nasara mai girman gaske ma kuwa, kai dai yi sauri mu isa gida kawai." karfe tara ya kawo su gida, Umma Karima ta shige gida tana jin kanta da girma. Da misalin karfe goma na dare Daddy na zaune yana dube-dube cikin computer. Mommy na zaune a gegen sa dan yau ita ce da shi. da sauri ya kai hannu ya dafe kansa tare da fad'in "Innalillahi wa innailaihirraji'un." ya rike kansa da karfe yana jin wani irin sarawa da kan sa keyi had'e da jiri da gilmawar bakin duhu. addu'a yarika karantowa duk wacce tazo masa baki. Mommy ta mike tana masa fifita da fad'in "Alhaji me ya faru?." yakai tsawon minti goma a haka da taimakon Allah da addu'a yarikajin sassaucin abin da yake ji. har ya iya janye hannunsa a kan da yake ji kamar an d'aura masa wani katon abu mai matukar nauyi. kallon Mommy ya yi dake tsaye tana masa fifita, numfashi ya ja da kyar yana tuna da Fad'imatu'n sa ce da da addu'a zata taimaka masa ba fifita ba. ido ya rumtse yana jin girman ta cikin zuciyarsa, lallai mace mai ilimi garkuwa ce cikin gida. Da kyar ya iya mikewa ya dawo bakin gado ya zauna, yana cigaba da ambaton sunan Allah. har yakai bayan sa ga katifa bai fasa ambaton Allah ba, yana ji kamar ana kafa masa kusosi cikin sassar jiki musan kansa da yake jin sa kamar zai rabe gida biyu sabar nauyi. yakai awa guda idanunsa a rumtse bawai ko dun ya yi bacci ba. Mommy kuwa ganin ya yi suru da addu'o'in da yake a fili, tuni ta d'ale gado tashiga sauke minshari. sai wajen karfe biyu kafin ya samu bacci marad dad'i ya d'auke shi mai cike da tarin wahala. kamar yadda ya saba munanan mafarkai masu cike da rud'ani da firgici yanzu ma haka ya soma, sai dai na yau ya girmi na sauran lokutan. Wasu halittu ne masu ban tsoro suke binsa zasu kamashi abaya gudu yake basa samin nasarar kamashi, yau kam duk iya gudun sa sai da suka cimmasa. suka d'ad'd'aure shi da igiyar wuta, jikin wani katon itaciya wacce kasan ta, rami ce mai zurfin gaske wuta yana ci ba kakkautawa. ga mashi gami da kifiyoyi a hannunsu suna ihu mai firgitarwa da haniniyar zasu kashe shi. ga igiyar wutan tana shiga jikinsa tana cin namar jikin sa. wad'annan dodannin halittun kuwa, sun d'aga wata kifiyar wuta suna daf da caka masa. ya zabura tare da yin salati ya mike zaune jiki na kyarma. ya had'a zufa sharaf hatta tafin kafarsa zufa yake. hannu ya kai ya dafe kirjin sa da yake ji kamar zasa fito. kallon gefen sa ya yi yaga Mommy na kwance tana sharar baccin ta. da kyar ya mike yana jin jiri na d'ibansa ya fad'a bayi ya yi al'wa ya fito. ya shinfid'a sallaya yasoma gabatar da sallah a daddafe. har wajen karfe hud'u ya sallame ya kwanta kan sallaya bacci na d'aukar sa yakuma yin wannan mafarkin. kiran salla ce ta taimake shi wajen farkawa daga mummunar mafarkin nan. ranar Daddy bai iya fita masallaci ba a gida ya yi salla. Mommy na idar da sallar ta taja kafarta ta koma side d'in ta, babu gaisuwa bare tambayar sa ya yakwana da jikin nasa. Daddy na zaune har wani lokaci a kan sallaya dare d'aya ya jijjiga har ya fara fita a hayyacin sa. ya mike da kyar ya nufi sashin Aunty. Aunty na zaune parlour tana saurarar karatun alkur'ani a TV ya shigo. duban sa tayi tana sakar masa murmushi, shima murmushin karfin hali ya yi mata. ta ce "Yanzu nake shirin zuwa sashin ka naga har wannan lokacin baka shigo ba, na ce ko lafiya." murmushin yakuma yi mata yawuce bedroom d'in ta. ta mike ta biyo bayansa, taga ya haye gado ya kwanta. rike baki tayi "Daddy kazo ka kwanta kuma bafa a nan kake ba." tayi maganar tana karasowa bakin gadon, ta zauna tana dubansa cikin kulawa. da d'an mamaki ta ware ido a kanshi ganin yadda fuskarsa ta zabge kamar dai mara lafiya. hannun sa ta ruko tana fad'in "Ya ya dai Daddy me ke faruwa ne baka da lafiya ne?." tayi maganar cikin nuna damuwa sosai. hannunta ya kankame yana gyad'a mata kain. gaba d'aya ta damu ta ce "Me ya same ka Daddy ba dai ciwon ka ba, sannu kaji yanzu ina ne ke maka ciwo, Abdurrahim ya sani kuwa? bari na kirashi ya zo ya duba ka." ido ya rumtse kana ya bud'e ya ce "Banyi bacci ba jiya Fad'imatu ina jin kirjina da kaina kamar zasu fashe." "Subhanallahi sannu Daddy, kuma kasha maganin ka kuwa, ko dai kwana biyu baka sha ne? bari na d'auko maka na nan kasha sai na kira Abdurrahim." ido ya rumtse yana jin yadda kai da kirjin suke masa. ta mike da sauri taje ta d'auko maganin sa datake ajiyewa a gon ta wanda idan yana gurinta da kanta take basa yake sha. ta had'o da gorar ruwa tazo ta bashi ya sha. ta mike tana fad'in "Bari na d'auko waya nakira Abdurrahim." ya ce "Barshi tukunna Fad'imatu idan bai lafa ba zuwa anjima sai a kirashi." kai ta gyad'a cike da matukar tausaya masa. ta gyara zamanta gefen sa tana ta yi masa sannu. ta bud'e tafin hannunta tana karanto addu'o'i ta tofa ta shafa masa a kai d'in zuwa jirjin sa. a hankali ya lumshe idanunsa yana jin nutsuwa na shigarsa, duk da yana jin ciwon amma yaji matukar jin dad'in nutsuwar da ya samu wanda jiya zuwa yau da safiya bai samu ba. a hankali a hankali bacci ya tafi da shi. ganin yasamu bacci Aunty ta tafi kichin domin ta shirya masa abincin da ta san yafi so idan ya tashi ya ci. ita da Feeryal da Baba Rabi ne a kichin. Feeryal na taimaka mata da wasu abubuwan in da Baba Rabi kuma ke ta aikin gogewa da wanke duk in da yab'aci da duk abin da akayi amfani da shi aka aje zata d'auka ta wanke ta goge sannan ta maida shi gurin zamansa. Suna kammalawa Aunty ta d'auko lafiyayyen girkin da tayiwa Daddy, Feeryal kuma ta d'auko nasu shima kayataccen breakfast da abinda tafi muradi wato cake d'in da ta had'a da kanta, da yoghurt mai sanyi. ta fito ta haura da shi dinning. Aunty na shiga ta hango Daddy jikin sa na b'ari ya had'a gumi sharkaf, idanunsa kuma a rufe. da sauri ta dire tray'n abincin hannunta kasa, da sauri mai kama da gudu ta hayo gadon ta rirrikeshi tana jijjigashi da kiran sunan sa "Daddy Daddy Daddy!." da karfi ya ware idanunsa da sukayi mugun ja ya sauke wani nannauyan ajiyan zuciya. ya kankameta numfashin sa na sama-sama ya ce "Fad'imatu zasu kashe ni!." a hargitse Aunty da kwalla ya fara zuba mata ta ce "Su waye Daddy ina suke!? innalillahi wa innailaihirraji'un." "Dan Allah Fad'imatu kar ki bari na sake yin bacci, ina kuma yin bacci nasan yanzu kam zasu kashe ni, kirjina da kai na zasu fashe Fad'imatu." Aunty data shiga mummunar tashin hankali hawaye d'aya na bin d'aya ta rungume shi tana fad'in "Bazaka mutuba Daddy bazaka mutu ba." ta mike da sauri ta fita ta d'au wayarta ta daddanna ta tura kira wa lambar Abdurrahim. wayar tayi ta ringing bai d'aga ba, takuma mai da kiran shima sai da yakusa yankewa kafin ya d'aga. murya a hargitse Aunty ta ce "Abdurrahim kayi sauri kazo ciwon Daddy ya tashi!." ta kashe wayar da sauri ta koma ciki. Daddy na zaune dafe da dai-dai kahon zuciyarsa d'aya hannunsa na dafe da kansa sai jan numfashi yake da kyar tamkar zai fita yabar jikin sa. Ba ayi minti 10 ba Abdurrahim ya shigo rike da jakar kayan aikin sa. yawuce bedroom d'in Aunty kai tsaye. ganin halin da Daddy yake ciki sai da ya firgitashi, sai dai bai nuna a zahiriba cikin gaggawa yasoma bashi taimakon gaggawa. ganin ya had'a allura yana shirin masa, Aunty ta share kwalla cikin raunin murya ta ce "Abdurrahim bazai sa shi bacci ba dai allurar ko, ya ce baya so ya yi bacci in dai zai sashi bacci kar kayi masa." "Dole ne sai an masa ana bukatar ya sami bacci yanzu." Aunty tayi shiru tana kallon Daddy daya lumshe isanunsa ya yin da bakin sa ke motsi da alama addu'a yakeyi. sai itama ta soma karanto ayoyin Allah cikin ranta. Feeryal ta fito daga bedroom d'in ta d'aure da towel a kirjin ta kanta babu d'anwali, ta nad'e gashinta ta tufkeshi a sakiyar kanta kamar Donut. kofar Aunty ta nufa ta d'aura hannu kan handle tana kokarin murd'a handle d'in cikin muryarta mai fita da yanayin shagwab'a takuma karo ainihin shagwab'ar ciki tana fad'in "Ammie wai yanzu ma sai na sa bra, ina breakfast fa bacci zanyi, Ammie kar na sa ko..." da sauri ta janye hannunta daga kan handle d'in jin an bud'o kofar tun kan takai ga rufa bakin ta. arba da tayi da shi ne ya sanyata had'iye ragowar maganar ta. ta matsa gefe ta bashi hanya yasa kai ya fita. Aunty ta ce "Feeryal koma ki sa kaya ga Daddy bayida lafiya." da sauri ta koma ta sako kaya ta zo d'akin Aunty lokacin har bacci ya d'auke shi. Aunty na zaune da kur'ani tana karantawa a dai-dai saitin kansa. wannan bacci ya yi shi cikin salama dan kuwa baiyi mafarkin ba, hakan kuwa baya rasa nasaba da karatun ALQUR'ANI da Aunty take a kansa. bata gusheba har sai da ya farka da kansa. ya damke hannunta cikin nashi yana mai dad'a jin girma da kaunarta cikin ransa. sannu tarika jera masa bayan ta taimaka masa ya yi wanka ta zubo masa abinci ya ci. Abdurrahim ya kuma shigowa duba shi bayan ya bashi wasu magungunan yafita. Ajmal ya kira ya ce yarika zuwa yana duba jikin Daddy'n a side d'in Aunty yana sanar masa yanayin jikin nasa, zai tafi asibiti yanzu. Ajmal dake sashin Hajiya ya mike da sauri yana tambayar dama Daddy'n bashida lafiya ne. kashe wayarsa ya yi batare da yabashi amsa ba. Hajiya da taji an ambaci Daddy ba lafiya itama ta mike da sauri tana cewa "Kai Ajimi Abubakar d'in ne ba lafiya?." ya ce "Eh Ya Abdurrahim ne ya kira ni wai naje narika duba jikin Daddy yana sashin Aunty." da sauri Ajmal ya fita hajiya tabi bayan sa tana fad'in "Au Abubakar d'in ba lafiya arasa wanda zai zo ya gayamin a cikin gidan nan akwai wanda ya haifa min shine, zancen banza kai." bala'i Hajiya tarika har suka isa sashin Aunty. Aunty na jiyo hayagagarta ta yi sauri ta fito tana fad'in "Hajiya sannu da zuwa ga Daddy'n ta nan." "Eh ba shakka anya Fatima ni da d'ana ma amma wai yana ciwo ban saniba kamar bani na haifa ba, kin kakabeshi cikin d'aki sai ya mutu tukun kifito min da shi, kice kwana ya kare ko me." Feeryal da ta mike zata shige d'aki ganin Hajiyar, karaf suka had'a ido aiba shiri ja ta tsaya cak....! Mommyn Twins ce 22 Hajiya ta yaguna fuska da baki ta ce "Um gayyar tsiya ana tare da mayu a gida taya za'a zauna lafiya." Feeryal ta sunkiyar da kai bata d'ago ba sai da Hajiya ta shige d'akin Aunty, kafin tayi hanzarin shiga bedroom d'in ta. Hajiya na shiga ta rike hab'a tana cewa "Kai Abubakar ya jikin naka, to mene ne amfanin kakabeka da akayi a cikin d'aki, kana kwance ciwo na karuwa babu sauki." ta kalli gefen da Aunty take ta kuma yaguna fuska tana cigaba da fad'in "Kazo ka kwanta a nan alhalin gacan uwargidan ka, in kwanciyar jinya ce idan bazaka iya yin sa a d'akin ka ba, sai kaje d'akin uwargidan ka, kafin ka fara sanin kowa ita ka fara sani, 'yar'uwar ka uwa d'aya uba d'aya da mahaifinta da naka, jinin ka ai sai yafi kula da kai fiye da bare, to banjiba ban gani ba ka tashi ka koma can shashin uwar gidan ka kaje kayi jinya, mu haka muka sani a hausance baza'a kawo mana wani iyayin zamani ba." Aunty tayi murmushi tare da girgiza kai. Ajmal ya ce "Haba Hajiya sai wani surutu kike ko a ina in dai jinya ce ai za'ayi, surutun nan na damin Daddy kiga yadda yake rumtse ido." "To ai sai ka rufa min baki ka hanani magana, ina ganin gaskiya a zane bazan sallaka ba." Ajmal ya masa kusa da Daddy yana masa sannu. sai a sannan ita ma Hajiyar ta maso tana cewa "Abubakar ya jikin naka abokin turawa ya baka magani kuwa, to ma wai ina yatafi ne kai kana nan a kwance, yaran yanzu wai tausayin iyaye ma babu a ransu, na dai gaya maka maza ka tashi ka koma d'akin uwar gidan ka, mu a al'adarmu ta hausa haka muka ni, miji ya yi jinya ad'akin uwar gida, kai dama Allah yasa 'yar'uwar ka ce uwar 'ya'yan ka." cikin muryar ciwo Daddy ya ce "To naji Haji amma anan nafi samu nutsuwa." "Nutsuwar hofi na dai gaya maka maza ka tashi ka tafi, kafin kasan nan d'in can ka fara sani, me ya kashe ka dacan, zancen banza kai, kana tare da mayu guri guda ina jiki zaiyi sauki." ta juya tayi waje tana masifa. Ajmal ya ce "Kai wannan mata akwai fitina, gara da kika tafi ma, ki bar mutane suji gari, Daddy ciwon kan na nan ko yana d'an sauka?." Daddy ya ce "Da sauki." Ajmal ya fita yana kiran Abdurrahim a waya ya sanar masa da sauki. Aunty dake gefe tana tsaye, Daddy ya kirata da hanu. ta karaso in da yake. ya ruko hannunta murya a raunace ya ce "Kiyi hakuri Fad'imatu." da sauri ta ta tare numfashin sa "Daddy gaskiya Hajiya ta fad'a can ne ya kamata ka zauna ba nan ba." "Kinfi so naje na mutu a can d'in bazaki cigaba da taimaka min ba?." kai ta girgiza zuciya cike da rauni ta ce "Bazaka mutu ba Daddy sai in kwanan ka ya kare, amma fa ka san da cewa idan bakayi abin da Hajiya ta fad'a ba za'a sami matsala." ido ya rumtse bai kuma cewa komai ba, tabbas anan ne kad'ai yasan zai rika samin sassaucin abin da yake ji. Akai-akai Ajmal ke zuwa duba shi kamar yadda Abdurrahim ya ce mishi. Aunty kuwa time d'in shan magani nayi zata bashi, bayan ta tabbatar da yad'an ci wani abu. Mommy ta tada bori in da akayi duniya bata yadda ba an d'au kwanan ta a kaiwa Aunty. taje ta sami Hajiya Hajiya ta taso ta shigo da bala'i tace dole sai Daddy ya tashi ya koma sashin Mommy, ai batasan yana nan ba tayi zaton ya tafi tun da safe. dole Daddy ya tashi ya koma sashin sa, sabo da masifar Hajiya, ta ce eh gara ya zauna a sashin nasa bazai zauna a gurin Aunty ba. har dare Umma Karima bata shigo ta duba Daddy ba tana can tana bidirin ta tana ta shirya yadda abubuwa zasu tafi mata yadda take bukata. Tun da dare ya yi hankalin Daddy ya yi masifar tashi, ko da Abdurrahim yazo masa allura ya ce kar yayi masa, yana fargabar kada ya yi bacci. Daddy ya yi ta iya bakin kokarin sa gani bai kwanta bacci ba, amma fa ina bacci b'arawo sai da ya sami nasarar sacesa. ai kuwa yasha fama cikin bacci, igiyar wuta tana cinsa suna daf da caka masa mashi. wani haske yazo yagilma a sakanin su, duk suka dare. daga can yaji ana cewa "Ka kamo haskem can kar kabari ya tsere kayi gaggawan taro shi, shine tsiran ka, ya zauna cikin rayuwar ka tanan ne zaka kub'uta, idan ya kub'uce shike nan babu tantama zaka mutu a wannan tsekon!." hasken yatafi can da nisa sannan ya juye zuwa mutum, sai dai an bashi baya baya iya ginin fuskar mutumin. yana b'acewa wad'an nan halittun suka kuma tasowa suka dawo suka cigaba da azabtar da shi. dakyar ya farka ya had'a zufa sharaf. ciwo ya dawo sabo. Mommy na d'akin amma bata iya taimaka masa da komai ba sai sannu da take ta jera masa. Har sai washegari Umma Karima ta shigo duba shi, ta koma da karfin gwaiwar ganin aikin ta na tafiya dai-dai yadda take so. A b'angaren Aunty kusan kwana tayi tana sallah da nima masa sassauci a gurin Allah. da sassafe taje ta duba shi ganin yadda yadad'a fita hayyacin sa. ta dawo sashin ta tashiga rusar kuka. waya ta d'aga ta kira Hajja Umma tana d'agawa takuma saka kuka, hankalin Hajja Umma yatashi matuka tashiga tambayar ta me yake faruwa, da kyar ta samu tayi shiru nan take gaya mata abin da ke faru. Hajja Umma ta sauke numfashi gwuiwa a sanyaye ta ce "Amma ni a gani na jinyar nan nasa a had'a da na gida, a gani ko za'a dace, Allah ubangiji ya bashi lafiya, bari Alhaji ya shigo zan sanar masa." Aunty ta ce to sukayi sallama ta kashe wayar. tausayin Daddy ya cikata ciwon kwana biyu ya jijjigashi ya fita hayyacinsa gaba d'aya. Motar Abdurrahim ne yashigo gidan. yana gyara parking ya fito yashiga sashin Daddy. ganin jikin Daddy na yau sai da jikin sa ya d'anyi sanyi, bayan ya bashi kulawar data dace ya fito ya wuce ide d'in sa. yana tsaye cikin bedroom d'in sa yana rage kayan jikin sa yaji an rungume shi ta baya. tawani lumshe ido cikin makirarren murya ta ce "Sannu da dawowa mijin Kuraiba an dawo lafiya ya aiki." ta dawo ta gabansa tana wani karairaya tayi sama da hannunta tana tayashi b'alle boturar rigarsa. tana gama b'alle boturan ta yi kasa da hannunta kan belt d'in wandon sa, tana kokarin kunce balt d'in. hannunta ya rike ya kauce gefe ya sa kai ya shige bathroom batare da ya ce da ita komai ba. bayan sa tabi da kallo tana ji kamar ta bisa cikin bayin. wani mika ta sake tana matse ido, yau ba karamin magunguna ta d'urawa cikin ta ba, ba'aje ko nan da can ba ta fara sakin layi. a hankali ta juya ta fita ta koma d'akin ta. wanka tayi tasa wasu arnan kayan baccin da babu marabar su da babu. ta jikin window ta hango shi yana fita daga side d'in, tasan gurin Daddy zai je ta sake labule taje ta d'auko wasu magungunan nata ta cuccusa a gaban ta. tana zama bada jimawa ba taji ana knocking. ta mike da sauri ta d'au after-dress ta saka kan kayan jikin ta fito, sai taji knocking d'in ta can ta kofar parlour'n sa ne. da sauri ta nufi parlour'n dan zaton ta shine ko kafar ta kulle ne dole sai an bud'e ta ciki. tana isa da saurin ta ta bud'o kofar da zummar ta rungume shi, sai ganin Ajmal tayi tsaye rike da d'an karamin flas da glass cup a hannun shi. murmushin yake tayi ta ce "Karamin ango ya akayi ne." washe baki ya yi ya ce "Matar yaya barka da dare ai naki shiga kai tsaye ne shiyasa nayi knocking." "Okay mene ne wannan d'in?." ta nuna flas da glass cup d'in hannunsa. ya ce "Sudan tea d'in Ya Abdurrahim ne ya ce nakawo na ajiye masa." "Okay to kawo mana bari na karasa da shi." ya mika mata ya yi mata sai da safe ta mai da kofar ta rufe. har zata haura stairs wani dabara ya zo mata, sai ta dawo da sauri ta nufi gefen ta, tana shiga d'aki, ta bud'e jakan magungunan ta ta ciro wani magani ta barbad'a a ciki ta mosa shi sosai ta mayar da murfin ta rufe. ta fita da sauri ta haura taje ta aje masa, ta dawo d'akin ta ta kwanta. Sai wajen 9 ya shigo ya tub'e jallabiyar jikin sa, ya zauna da gajeren wando. ya d'au flas d'in ya tsayaya tea d'in cikin glass cup d'in, kana ya soma sha a hankali. sai da ya kai karshe yaji d'and'anon sa ya babbanta dana kullum, ido ya zubawa kasan cup d'in ganin abu ya kwanta a kasan shi. juye sauran tea d'in ya yi nan yakuma ganin da alamun abu a ciki. ya janyo wayarsa ya kira Ajmal, yana d'agawa ya ce "Ina tea d'in baka karb'o bane?." da sauri Ajmal ya ce "Tun d'azu na karb'o Kuraiba ta karb'a ta shiga maka da shi." kashe wayar ya yi batare da yakuma cewa komai ba. ya mike yaje yaja bedside ya d'au wani table yad'au gorar ruwa ya b'are ya sha. kana ya haye gado ya kwanta, bayan ya yi addu'a. Kuraiba da ya shigo a kan idon ta bata fita ba sai da karfe 11 ya cika, lokacin itama ta gama jika ta tsumama. ta mike cike da confidence ta nufi saman shi. Tayi mamakin ganin sa kwance da alama bacci yake. dan maganin da ta saka masa bai isa ya iya rumtsawa ba idan bai kusanci mace ba. ta tako ta haye gadon ta shige jikin sa gaba d'aya ta narke, dan a mugun hanu take. tashiga shafashi tana kokarin tura hannu cikin wandon shi. ya yi saurin ruko hannunta ya ture ta a jikin sa. tare da buga mata tsawa "Ta shi ki fice min anan!." kamar zata fasa kuka ta koma tana fad'in "Mijin Kuraiba please and please kar ka koreni ajikin ka, I really love you dan Allah." a haukace takuma rungumo shi tanajin yadda kasanta ke motsawa yana niman mai agazama masa. ido ya kura mata ganin yadda ta birkice gaba d'aya yana hango tsantsan bukata tare da ita. gani ya yi shiru bai kuma tureta jikinsa ba. gaba d'aya ta birkice masa tana safashi da kissing d'in sa. sai da ya tabbatar da ta kai kololuwa pant d'in jikin ta ya gama jikewa. ya mike ya bata guri, ya yi mata alama da hanu ta tashi ta fita. gaba d'aya idanunta ya rufe ta mike takuma fad'o wa jikin sa tana sakin wani numfashi da kyar ta iya furta "Dan Allah kar kayi min haka Abdurrahim, hakkina dake kanka idan ka danne bazan yafe ba." buga mata tsawa ya yi fuska ba wasa ya ce "I say get out!." jikin ta ya kama rawa dan ba tsawan wasa ya yi mata ba. ta fashe da kuka ta kuma fad'awa jikin sa dan wlh tana jin sha'awar da zai iya hallaka rayuwar ta. rigar jikin ta ta yaga nonuwanta da suka fara zubewa suka bayyana dan ma suna samin gyara dad'an fasalin su. ta manna su a jikin sa cikin muryar kuka a rikece ta ke fad'in "Saboda son da nake maka yasa na kawo kaina gareka shine kake min wulakanci, duk wani wulakancin da kake min sai na kira Mommy na gaya mata." Kamar ya yi mata d'na banzan duka haka yake ji, badun gudun abun da Mommy ta fad'a ya kama sa ba da yau sai ya tattakata. ya fincike ta a jikin sa ya tureta har sai da ta garu da jikin gado, ya ce "Oya je ki gaya mata." jan kafa ta shiga yi da kyar ta fice a d'akin tana ji kamar zatayi hauka sabar wutar jarabar dake azalzalarta ta kasa. tsaki yaja ya koma ya kwanta... duk yadda taso gusar da sha'awan ta da kanta ta kasa haka ta kwana birgima. Washegari da safe ya yi shirin tafiya asibiyi, yaje ya duba jikin Daddy bayan ya gama duba jikin nasa ya basa magani ya yi masa allurai. jiki a d'an sanyaye ya fita dan lamarin jikin Daddy'n kullum dad'a kara gaba yake. a parlour'n Daddy ya had'u da Mommy data shigo yanzu. ya gaisheta batare da ta amsaba ta bishi da wani kallo, cikin kasa da murya dan da mutane cikin parlour'n ta ce "Idan bakaji tsoron Allah ka sauke hakkin da yake kan ka ba, wlh bazakaga dai-dai ba, kuma wlh ban yafe maka ba, baka isa ka kunyata ni ba." ta wuce bedroom d'in Daddy. har ya ja mota yabar gidan yana mamakin yarinyar wato da gaske karan nasa takai akan yaki kusan tarta, lallai wannan yarinyar tacacciyar mara kunya ce. a daren ranar kuwa sai da ta maitance da naciya da kafiya ta samu abin da take so, ba dan son ransa ba... Wasa-wasa ciwon Daddy sai gaba yake, kullum ba sauki, gaba d'aya ya rame yafita hayyacin sa. kullum dare kamar sotse soka da jinin jikin sa ake. Aunty ce ta fito da ga bedroom d'in ta da sauri, zataje duba in da Daddy ya kwana da jiki. Feeryal ta ce "Ammie ki jirani muje na gaida Daddy." Aunty ta nufi kofa da sauri tana fad'in "Feeryal ki same ni acan." tayi waje da sauri dan jiya da shi ta kwana aranta. ganin Aunty tayi gaba sai ta koma ciki, da ma batayi wanka ba. sai da tayi wanka ta shirya cikin riga da sket na atamfa ta d'au bakin gyale ta yafa kana ta fito. can ta hangi Miemie daf da side d'in Daddy suna tsaye ita da Sumayya. A hankali take takowa cikin yanayin ta mai sanyi. Zaraddin da abokin sa Ziyad suna tsaye a bakin get d'in side d'in su, a jikin motar Ziyad d'in. Ziyad na hango ta ya kafe ta da ido yana fad'in "Wow See beautifully, kai kaga wata 'yar shila kuwa, irin wannan kayan marmari haka, kai Deen wai wannan kayan alatun a gidan nan kuke rayuwa da ita, kai narantse har naji abin na na motsi." Zaraddin da shima idanun sa a kan ta ya yi wani murmushi mai kama da dariya yana shafa gefen fuskarsa ya ce "Zazzafa yarinyar mai zafi ce, mallaki na ce ita d'auke idanunka a kanta, matar da zan aura ce." "Kai wai da gaske kake ko wasa." Zaraddin ya ce "Da gaske nake auren ta zanyi, idan na aje wannan a gida ta ishe ni komai, babu wata macen da zan kuma kulawa, idan wannan tana gefe na zan koshi har wuya." "Amma kam taji kayan had'i, to kafin ka d'auke ta zaka bani aron ta na kwana d'aya kawai, ba'a hana mabada rago fata ka sani." harararsa ya yi yana jijjiga kai idanunsu duk a kanta.. Ta karaso gurin su Miemie. Miemie ta rike baki ta ce "Iyee kinga kyan da kikayi cikin atamfa kuwa." murmushi tayi mata, Sumayya ma ba yabo ba fallasa ta ce "Sannu Feerya." itama ta ce "Sannun ki." ido Sumayya ta waro ta ce "Nashige su gashi can shigowa, jiya yace na kunce kitson attach d'in nan, ban tsefe ba bari naje na tsefe yanzu kafin mu had'u." Miemie da Feeryal duk suka juya in da take kallo. ya shigo a kan keke yana sanye da wando da rigar Jecy yellow, kafarsa d'aure da farin takalmi sau ciki, da dogon safa. Miemie ta ce "Ya Abdurrahim nefa ya fito motsa jiki ke nan, Allah yasa ya zo ya tare ki a nan." "Ai bazan ma tsaya ba d'akin Hajiya zanje na tsefe acan." ta juya tayi gudu ta tafi sashin Hajiya. suma suka shige sashin Daddy. Ziyad ya shige motarsa ya na fad'in "Deen kar ka mance dai 1 za'a tafi club d'in nan, ka taho mana da wancan zazzafar zata kayata gurin." kafin Abdurrahim ya karaso gurin Ziyad ya tada mota ya nufi get. yana karasowa yabi Zaraddin da wani kallo. Zaraddin ya d'an sosa keya yana cewa "Bros an dawo." fuska a suke babu damshin annuri ya ce "Kar ka sake shigo da shi gidan nan, kar na sake ganin sa a cikin gidan nan......! 23 "Nayi maka magana kan harka da yaron nan baka dai na ba ko." ya yi maganar yana dad'a tamke fuskarsa. Zaraddin yakuma sosa keya yana fad'in "I'm sorry bro." kai ya jinjina ya wuce kan keken sa zuwa b'angarensa. A parlour su Feeryal suka tsaya sabo da wasu 'yan'uwan Daddy dake tare da shi a bedroom d'in shi. sun b'ata lokaci kafin suka fito, nan suka sami damar shiga duba shi. jiki a sanyaye Feeryal take gaida Daddy ganin jikin nashi sosai ne. murmushi ya yi mata yana amsawa da kai. Aunty na d'akin tana ta faman gyara in da aka b'ata, Umma Karima ta shigo tabi Feeryal da kallon banzan. tana cewa "Tun da anyi gaisuwar sai a tashi aje ba zama ake yi ba, ya kamata ma fa a hana masu shigowa gaisuwar nan haka bamusan da me ake shigowa ba, ba 'yan waje kad'ai za'a hana su shiga ba har da wanda suke gidan, ana jinya amma kullum ciwo gaba ya ke, waya sani ma ko ana tufka wasu na warwara ne." Aunty ta ce "Idan ma tufkar ake daga gefe ana warwara insha'allah Daddy zai sami lafiya, kullum fatan sauki muke nima masa." Umma Karima tabi Aunty da kallon banza tana cika tana batsewa ta isa ta hakimce kan kujera. tana fad'in "Magana nake kan b'aren da suke cikin gida masu shigowa kan sa, bamu yadda ba idan ba na jikin sa jinin sa ba babu mai kuma zuwa duba shi, za kuma ayi Meeting akan haka." Aunty tayi kamar bata jita ba dan tasan niman magana take ita kuma bazata biye mata ba damuwar ciwon Daddy ma kad'ai ya ishe ta. Miemie ta janyo hannun Feeryal sukayi waje. a bakin kofar parlour'n Daddy ta tsaya tana fad'in "Wlh matar nan nakusa na tsaya na wanke ta daga sama har kasa, rashin mutuncinta karuwa yake dad'ayi." Feeryal tayi murmushi bata ce komai ba dan tasan da ita Umma Karima take. Kuraiba suka hango tana zuwa, wasu masassun kaya ne a jikin ta, sai wani d'an misitsin gyale data rataye shi a gefen kafad'ar ta. da wani takalmi mai tsinin gaske a kafarta, ta toshe ido da bakin glass tana taunar cingam. "Um kaga amarya ansha gayu wane za'aje club, kuma wai an zo gaida siriki ke nan." cewar Miemie tana mara baki. Feeryal ta kalli Kuraiba sannan ta maida kallonta ga Miemie ta ce "Ai kuwa tayi kyau." da sauri Miemie ta ce "Dalla ina wani kyau anan tana tafiya kamar agwagwa, ni har tama ban haushi." "Ke Miemie Allah ba ruwana taho mu tafi." Feeryal ta ruko hannun Miemie tana kokarin janta dai-dai san Kuraiba take karasowa kofar parlour'n. yatsa ta saka ta d'an ture glass d'in idon ta sama, tana wani taunar cingam yana kas-kas. ta bisu da wani kallon rashin daraja sannan ta ce "Ku ta ina kukaga mijin Kuraiba ya shige?." Miemie ta mayar mata da irin kallon da ta musu sannan ta ce "Waye kenan me irin wannan sunan sai dai ki shiga ciki ki tambaya." mai da gilashin tayi ta gyara zaman sa a idon ta, ta buga cingam d'in ya bada kara kass. har sai da hankalin mutanen dake cikin parlour'n ya dawo gurin su, kana tayi musu kallon sama da kasa tacikin glass, sannan ta sa kai ta shige ciki. da sauri Feeryal ta ce "Miemie ba sunan ta ba ke nan Kuraiba? to ai mijin ta ke nan ta ke nufi." "Na gane sarai 'yar rainin hankali mu zata gwadawa iyayi, wai wani mijin Kuraiba to ai ko bata fad'a ba ai ansan mijin ta ne, ni bana son mutum mai iyayi irin haka, ita gatanan me miji, ai sarai naga shigowar Ya Abdurrahim d'in ta can kofar ba gashi can ba tsaye da uncle Bashir, dubi yadda ta nufe su ni fa haushi ma tafara bani, ni na tsani macen da batasan kanta ba, dan kayi karatu a kasar waje sai ka zamo mara jan aji a matsayin ka na mace, komai ka nuna wayewa kawai, ai badun ciwon Daddy ba muma da last year zamu bar kasar, amma wlh sai dai ma na rike kaina narika jin kaina a big girl, ni zo mu tafi ma dan Allah naje naji muryar Murad d'ina zuciya ta tayi sanyi." ta janyo feeryal suka fice. Zaraddin ya shigo parkour'n Mom tana zaune ita da Shamsuddin. Mom ta bishi da kallo har ya zauna. ya kalle ta yana shirin yin magana Mom ta ce "Ya akayi ne Zaraddin?." ya ce "Mom aure nake so." cikin farinciki da jin dad'in fitar kalmar aure daga bakin sa ta ce "Kai nagode Allah shike nan kayi auren ma ka huta da bakin mutane, sai su karaci mugun bakin su ta wani gurin, ka sami matar auren ce, wace yarinya ce wane ne uban ta a garin nan? ai kuwa ko wata baza'a kai ba zayi auren nan." Mom gaba d'aya farinciki ya lullub'e ta Zaraddin d'an gaban goshin ta da kansa ya ce yana son aure yau, wan da tuntuni Dad ya ce ya fidda mata ya yi aure maganganun mutane sun dame sa a kan halinsa. ya ce shi bai ga matar aure ba. ya ce "Mom a cikin gidan nan take kuyi-kuyi magana kawai ku aura min ita, yanzu nake son a aure min ita, idan ba'a aura min ita bafa za'a sami matsala." Shamsuddi ya dube sa yana fad'in "Yanzu kai Daddy na kwance ba lafiya kake maganar kana son aure yanzu-yanzu da wurwuri, ta ya za'ayi aure a gidan nan yanzu Daddy yana kwance ba yi da lafiya, ka daiyi tunani ka bari idan ya sami sauki koma meye sai ayi." Zaraddin ya harare sa ya na cewa "Sai me ciwon nasa zai hana a d'aura aure ne, abun da za'a tara mutane kawai a shaida shine me." Shamsuddin ya girgiza kai tare da fad'in "Allah ya baka sa'a." Mom ta ce "Uhum yanzu kayi magana dan wani ba lafiya in dai ba ango ko amaryar bace ai ba wani abin tashin hankali bane, bari Dad d'in ku ya shigo muyi maganar, a saida rana karshen wata ayi biki, wace ce cikin su Bilkisu Saddiqa Nabila Sumayya Miemie ko Ameerah?." Zaraddin ya ce "Ina duk ba su ba wancan kyakkyawar Feeryal dai." wani irin d'agowa Shamsuddin ya yi. Mom ko korji ta dafe a tare suka furta "FEERYAL!." Zaraddin ya ce "Eh ita ita nake so idan ba ita ba babu wata macen da zan aura, kawai a bani ita idan ba haka ba." ya wani girgiza kai. da karfi Shamsuddin ya mike ya nuna shi da yatsa ya ce "Karya kake Feeryal bata dace da kai ba." Zaraddin ya mike yana cewa "Idan bata dace dani ba da wa ta dace, ita nake so kuma sai na aure ta." "Dani ta dace ba da kai d'an kwaya ba, Feeryal tawa ce." da karfi Zaraddin ya shako wuyan Shamsuddin ya ce "Idan ban kashe kaba na nuna maka halin kwaya anan, idan ka sake cewa Feeryal taka ce idan ban bubburma maka wuka ba." Shamsuddin shima ya cukime shi yana fad'in "Mu burmawa juna wuka dai, duk iskancin ka ka isa kayi min na kyale ka ne, na fad'a baza a aura maka ita ba, kayi abin da zakayi." da sauri Mom ta shiga turesu tana fad'in "Bakuda hankali ne yanzu akan mace kuke fad'a, macen ma aljanar ruwa, to duk cikin ku babu shegen da ya isa ya aure ta, baku isa ku auro min wancan bakar mayyyar aljanar ba." Shamsuddin ya sake shi ya juya da sauri ya nufi kichin yana fad'in "Zakaga abunda zan yi a kan ta kuwa." Mom ta sa hanu a kai ta yi kiruru tana fad'in "Wayyo Allah tambad'ad'd'iyar yarinyar can ta had'a min yara fad'a zasu kashe kansu." Zaraddin ya fito da wuka ya yi kan Shamsuddin. Dad da shigowar sa ke nan ya buga masa sawa. "Zaraddin! kar ka soma." da sauri Mom ta shiga sakanin su hannun ta akai bata fasa kururuwa ba. da d'ebewa Feeryal albarka ba. Zaraddin ya saki wukan kasa yana huci ya ce "Wallahi da na nuna maka halin kwaya Feeryal kuma ni zan aureta ba kai ba." Dad yakuma buga musu tsaya "Banzaye shashshun yara, yan zu akan mace kuka shirin kashe kanku, ina ta son ganin rayuwar ku yaci gaba ina son ganin komai ya juya ya dawo karkashin mu, amma kun tsaya shashanci, barsu su kashe kansu." Zaraddin ya juya fuu ya yi waje yana huci. Miemie dake tsaye bakin kofa rike da kula Ammah ta aiko ta ta kawo wa Mom ta tsaya tana kallon ikom Allah. ai tana bata kular ta juya. in da tabar Ammah da Faisal nan ta same su, ta karaso baki na kaikayi na son bada labari. ta zauna tana rike hab'a da fad'in. "Cafd'i jam da yau anyi kisa agidan nan." Ammah ta waro ido ta ce "Kisa kuma?." Faisal ya ce "Ji wannan makaryaciyan ai ke narantse Miemie kin shiga uku da baki." ya yi maganar yana kai mata bugu a baki, ta kauce tana fad'in "Wallahi da gaske ne Ya Zaraddin da Ya Shamsuddin suke fad'a, Ya Zaraddin har da d'aukan wuka wai zai kashe Ya Shamsuddin, wai kuma kasan akan wa suke fad'an? akan Feeryal jifa wai duk suna sonta." Ammah ta ce "Ikon Allah lallai yarannan basu da hankali shine har da d'aukan wuka." Faisal ya yi shiru kamar ruwa yaci kansa. Miemie ta kalleshi ganin yadda jikin sa ya yi sanyi ta ce "Ai kaima Ya Faisal tuntuni na gama gano ka kaima sonta kake, Feeryal dukkanin ku baku da ce da ita ba." hararar ta ya yi ya ce "Ke ina ruwan so da wani dacewa ko rashin sa, da Ammah zataje ta sami Aunty nasan da za'a bani ita." "Babu in da zani ma duk kuje ku nimi matanku a wani wajen." cewar Ammah. Miemie ta fashe da dariyar ganin yadda ya wani narke murya kamar maraya. ya bita da hanu ta mike da gudu ta shige d'aki tana dariya. Da sauri Umma Karima ta shigo sashin Daddy, lokacin ana daf da kiran sallar magriba. tasan yanzu kowa ya koma sashin sa, Ajmaal da yake kwana tare da shi ma yanzu ya fita shirin zuwa masallaci. Daddy na kwance kan sallaya yana zaman jiran a shiga sallah ya mike ya gabatar. ta shigo ta hakimce kan kujera ta ce "Tashi Alhaji muyi magana." nan da nan ya aiwatar da abun da ta ce ya mike ya zauna. zama ta gyara tana kallon shi sannan ta ce "Ina takaddun kadarorin ka suke ina so ka tattaro su duka ka bani, yanzun nan." ya ce "To Hajiya Karima amma basa d'akin nan, ni da Abdurrahim ne kad'ai muka san in da suke, gashi ni bani da lafiyan da zan iya zuwa na d'auko miki." ta ce "Kira shi Abdurrahim d'in yanzu kace ya taho da su." ta d'auko wayarsa ta mika masa bayan ta danna kira wa lambar Abdurrahim. ya yi ta ringing har ya yanke ba'a d'aga ba. takuma mai da kiran a karo na biyar shima har yakusa yankewa kafin aka d'aga. da sauri ta saka wayar a amsa kuwa ta mika masa. daga cikin wayar aka ce "Ayi hakuri ranka shidad'e Sir yana Operating room yana surgery." karb'ar wayar tayi ta kashe sannan ta ce "Yana dawowa kasashi ya kawo maka a daren nan, zan zo na karb'e su da safe." ya ce To. ta mike ta fita. Bayan sallar isha Aunty Ammah Mommy Mom Hajiya, da 'ya'yan su. duk suna cikin parlour'n Daddy, in da Abdurrahim da Abbie da Dad suke ciki tare da Daddy dan yau jikin nasa ya tashi fiye dana kullum. Aunty dake zaune tayi jugum, sai addu'a take cikin ranta. gaba d'aya hankalin ta baya jikin ta yana gurin Daddy, sai kwalla take ta sharewa a b'oye. Aunty ta nisa ta ce "Hajiya nace ko za'a kai Daddy gurin magani ne a d'an tab'a na gida, a had'a jinya biyu ko Allah zai sa aci karfin lamarin." "Ba ke zaki bada wannan shawarar ba mu zamu yanke." cewar Umma Karima da ke shigowa parlour'n maganar Aunty ya dira a kunnenta. ta karaso ciki tana cigaba da fad'in "Mu masu 'ya'ya da mukasan zafin sa mu zamu yanke hakan, bake da bakisan zafin sa ba, sabo da kin raina kulawar da Abdurrahim yake bashi, likitan da likitotin kasar waje suka yadda da aikin sa fiye da nasu, yake jinyar sa shine zaki kushe kokarin sa, to mu masu 'ya'ya mun yadda da aikin sa bamu yarda akai shi wani guri ba, ke da baki haifi ko d'an hanji da shi ba baki isa ki rika nuna mana yadda zamuyi ba." Aunty ta girgiza kai tana murmushin takaici ta ce "Idan ma tunanin ki hakan nake nufi Abdurrahim yakasa kula da shi, to kicigaba da sawa ranki hakan, sannan baki da ikon hanani magana akan Daddy, yadda kike auren shi haka nima nake auren shi, 'ya'ya kuma wannan kin shiga hurumin Alla dan shi ya tsara hakan, dan Allah Hajiya Karima ki barni naji da abin da ke dami na." Aunty ta karasa maganar tana had'a hannayen ta biyu zuciyar ta na d'aci. Mommy ta ce "Mttss aikin banza sai arika nuna an fi kowa damuwa da Alhaji, idan gurin magani ne ma ina ne za'a kai shi, a fidda shi makiya su ji dad'in samin galaba a kanshi." Hajiya ta ce "Eh to nima dai zuwan Baba Salehu na Yelwa kafin su koma yake min maganar ko za'a had'a dana gida ne, sai a gwada a gani baza'a fasa na asibitin bama." Umma Karima tayi saurin cewa "To idan ma za'a had'a dana gida mu bamu amince a d'auke shi a kaishi ko ina ba, sai dai a kira mai maganin yazo gida nan, kuma mu zamu nemo mai maganin idan akayi ba'a dace ba sai ta nimo nata, ko ba haka ba Hajiya Halima?." Mommy ta ce "Kwarai kuwa." Hajiya ta ce "To ai shike nan mudai sauki muke fata masa, sai ki kirashi mai maganin yazo gobe idan Allah ya kaimu, idan baiyi ba ni da kaina zan d'auke shi mutafi Yelwan Shendam, abokin turawa yaje yana masa nasa jinyar ana kuma na gida, ni wannan ciwo na Abubakar ma yana min kamar aljanu ne, amma dai mai maganin yazo dai mu gani." kowa yarika tofa albarkacin bakinsa a gurin Aunty bata kuma cewa komai ba. tana rayawa a ranta ita da kanta zataje ta karb'o masa magani tazo ta masa. su Abdurrahim suna fita ta shiga. batabar sashin ba sai kusan karfe 1 bayan tayi masa addu'o'i ta shafa masa. Washegari Aunty tana idar da sallah taje ta duba Daddy, tayi mamakin ganin sa har lokacin yana bacci. Ajmaal ya ce mata ya tashi ya yi sallah yakuma komawa ne. ta tofa masa addu'a kana ta koma sashin ta ta soma had'a masa gwaten acca, wanda shi ne yanzu yake d'an iya ci. Wani irin zabura Feeryal dake bacci tayi. da karfi ta ce "Ammie kar ku barshi ya shigo gidan nan!." Aunty da ta fito rike da basket mai d'auke da abincin Daddy ciki, cikin hanzari ta shige bedroom d'inta. akwance ta isketa idanunta a rufe da alamu dai bacci take. Aunty ta juya tana kokarin fita. taji an kuma fad'in "Kar ku bari ya shigo gidan nan!." da sauri Aunty ta juyo, jin wani irin murya ne ya yi maganar ba irin na Feeryal d'in ba. ido Aunty ta waro ganin yadda jikinta ke jijjiga hatta gadon jijjiga yake, tamkar zai karye. kafin tayi aure tayi wani irin mikewa tsaye da kafafunta a kan gadon. cikin wani irin hargitsastsen murya ta ce "Kar ya shiga ya dakata a gurin!!." tayi maganar tare da fasa wani irin kara mai firgitarwa. da sai da gidan gaba d'aya ya d'auki amon sautin mai tarin tsoratarwa da rikitarwa. kafin Aunty ta ankara har ta duro a gadon tayi waje a guje. Aunty ta bi bayanta tana kira dan kayan bacci ne riga da wando a jikin ta. Umma Karima da me maganin da ta kawo suna daf da shiga side d'in Daddy. Feeryal kamar mai gudu kan walkiya ta iso gurin, wani irin damka tayiwa rigar sakin da ke jikin sa ta baya, ta finciko shi kamkar kwali ta d'auka ta jefashi can ya fettu da jikin garu. ta saki wani irin. haniniyar ihu, tayi kansa ta mika hannu zata damko shi......! Mommyn Twins ce Da karfi aka rike hannayenta duka biyu ta baya, tayi wani irin ihu tare da kokarin fisgewa. tana wani irin gurnani tana sunkoyowa kan boka Mali, ya yin da fuskarta ke rufe da gashin kanta. Abdurrahim ya yi baya tare da kuma janyo hannayen ta daya rike duka biyu ta baya, har sai da bayan ta ya garu da kirjin sa. da sauri boka Mali ya dafa jigin bango ya mike ya tattari kwaryar da ya toho da shi a hannunsa wanda sanadin feud'e shi da akayi jikin bango ya tarwatse. yashiga tattara fasassun da sauri jikin sa na kyarma. Feeryal na ihu tana tuma niman kwacewa a hannunsa tayi kan boka Mali. ai yana gama kwashe fasassun kwaryar ya d'au sandarsa ya zura a guje. Umma Karima ta bi bayansa tana kira tuni yafita a gidan da mugun gudu. Aunty ta sa hannu a kai tana salati ganin yadda Feeryal take niman kwacewa a hannunsa. tuni ya murd'eta ta zube kasa ya danneta. kana ya shiga karanto wasu ayoyi daga cikin alkur'ani yana tufa mata. Umma Karima ta dawo da sauri kamar hauka sabon kamu, tana fad'in "Gantalalliya asararriya kin fasa kwaryar hankalin ki ya kwanta." A ciki kuwa Daddy na kan azabtuwa cikin bacci. yau abubuwan da yake gani masu firgitarwa da ban tsoro sunfi na kullum. wannan hasken da yake zuwa taimakon sa cikin bacci shi yakuma zuwa a yanzu ma, dai-dai sanda aka danna masa mashin wuta a kahon zuciya ana daf da burma masa. wannan hasken ya bayyana. hasken ya tarwatse halittun, da suke zagaye da Daddy suna azabtar da shi. kana hasken ya wuce. daga can ya soma jin muryar da ke magana a duk san da hasken nan ya gifta. "Kar ka bari tayi nesa da kai ka janyo hasken can cikin rayuwar ka, idan yau ka kub'uta gaba ba lallai ne ka kub'uta ba, tabbas za'aga bayan ka, kar ka bari ta yi nesa da kai ka janyo sa cikin rayuwar ka, ana daf da ganin bayan ka, hasken kub'utar ka ce ka rike ta kar ta tsere daga rayuwar ka!!." da karfi yake jijjiga daga d'aurin da akayi masa, da igiyar wuta, dake shiga sokar jikin sa. yana ta fafutukan niman ta inda zaiyi ya kunce ya juya yaga hasken kub'utar sa. Su Mommy Hajiya da ihun Feeryal tun na farko kafin ta iso gurin ya fito da su daga sashin Daddy. Mommy da jike ke rawa ganin tashin hankali a idon ta ta ce "Wannan yarinyar ban yarda da ita ba, ke nan jinyar Alhajin ne bata so ayi, saketa ta tafi duk in da zataje Abdurrahim!." Hajiya kuwa kirji ta buga ta ce "Yau naga siddabaru to baza'a kawo min tashin bori cikin gidan d'ana ba, daina tofa mata addu'ar nan abokin turawa jata ka fita mana da ita anan." Aunty ta maso da sauri hankali tashe ta ce "Dan Allah Abdurrahim ka tai make ni ka kaimin ita side d'i na, dan Allah." ta had'a hannayen ta biyu. baiyi magana ba har ya kai karshen ayar da yaja. ya d'ago yaga kaf 'yan gidan maza da mata idanunsu a kan su, Zaraddin na ta gaba-gaba ya kafe ababen kirjinta tarr da ido. wan da babu bra iya rigar baccin ce mai tsamtsi a jikin ta. daga kasan rigar ma yad'an bud'e har kusa da cibiyarta, ana ha hango farin fatar shafaffen cikin ta. da hannu ya yi musu alamun kowa ya watse. Zaraddin yad'an sosa keya yawani lumshe ido tare da jan numfashi. yana jin hannunsa na kaikayi ina ma ace yaje ya damki balambalon kirjinta. "Daddy Daddy! innalillahi wa innailaihirraji'un Mommy Hajiya kushigo kuga yadda Daddy yake yi Ya Abdurrahimmmm!!.." Ajmaal ya ke fad'i a gigice ganin yadda jikin Daddy'n ke jijjiga kamar wanda aka jona da wutan lantarki, ya had'a gumi daga kai har tafin kafafun sa. Da karfi Daddy ya dafe kahon zuciyarsa har lokacin idanunsa a rufe ya kasa farkawa daga baccin da yake, sai da hasken ya yi nesa da shi kafin ya juya izuwa halittar mutun, yana daf da b'acewa ganin sa sannan ya juyo garesa, annuri shinfed'e a fuskarta tana murmushi kamar ko da yaushe a cikin rayuwarta. tayi jifa da hannunta ya isa ga inda Daddy yake. a take igiyar wutan dake tabaibaye da shi ya b'ab'b'alle ya zube kasa. wani katon kasko yafashe ya tarwatse. "FEERYAL!." Daddy ya ambata cikin baccin amma sai da lab'b'ansa suka motsa. Hajiya Mommy Aunty har suna rige-rigen shiga sashin Daddy jin kiran da Ajmaal ya ke. Abdurrahim ya mike tsaye daga sunkuyon da yake rai b'ace. ya fincikota ya mikar da ita tsaye, ya janyo ta tana tirjewa, ya yi da ita sashin Aunty. yana zuwa bakin kofar parlour ya turata ciki. ta zube kasa ta kuma yunkurin tashi. rai b'ace yasa kafa cikin parlour'n tare da d'auke ta da mari ta kuma komawa tayi flat a kasa. cikin kakkausar murya ya ce "Idan kuka kuma fitar da ita da wad'an nan kayan na rantse sai na kashe ku!, kar ku kawo wa mutane iskancin banza a gida." jikinta ya sake gaba d'aya, ta ja numfashi mai d'an tsawo kana ta shiga sauke numfashi a hankali a hankali idanunta a lumshe, sai kawai ta gyara kwanciya taci gaba da baccin ta. tsaki yaja yana d'auke idanunsa a kanta. ya juya har yakai bakin kofa sai ya kuma juyowa ya dawo. hannun rigarsa ya gyara ya sunkuya ya sa hannu ya d'agota cak. wani irin bugawa kirjinsa ya yi sanda yake had'a ta da jikin sa. a hankali ya shiga d'aga kafarsa yana nufar bedroom d'in ta da ita. ajiyan zuciya mai sauti ta sauke, ta dad'a manna kanta a kirjin sa, tana kara lafewa cikin jikin sa. hannun guda ta sakalo wuyan shi, d'aya hannun nata kuma ta tura ta bayanshi ta kankame rigarshi ta baya. da d'an sauri ya kalli fuskarta bacci take da gaske. yana isa bakin gado ya cirota a jikin sa ya wurgata kan gadon yana gyara zaman rigarshi baki ta cuno har lau udanunta a lumshe. cikin siririyar muryarta mai cike da bacci ta ce "Ammie kaina ciwo." sai kuma ta gyara kwanciya tayi d'ad'd'aya da kafafun ta, rigarta duk ya tattare ya koma sama gaba d'aya cikin ta yana waje. da sauri ya yuya yafita yana mai dad'a jan tsaki. ya janyo mata kofar. acan wajen sakar gidan ya ga Miemie ya kirata ta karaso in da yake da sauri. ya ce "Je ki same ta tana." yana fad'in haka ya juya ya nufi sashin Daddy. Yana shiga d'akin Daddy ya ja ya tsaya daga bakin kofa yana kallon Daddy dake zaune, su Hajiya suna zagaye da shi, kowa bakin sa yakasa rufuwa. Hajiya na ganin sa ta ce "Kai abokin turawa kai ma mamaki kake na ganin sa zaune, yana magana tiryan-tiryan kamar bashi ne ke kwance d'azu shame-shame rai a hannun Allah ba, har waje na fita duba ka kazo kaga halin da yake ciki amma ban ganka ba, uban ka yana nan a kwance kai katafi taran aljanu 'yar da ta so kashe mai magani, ina zaka iya da ita, irin wannan jifa da tayi da shi Allah kad'ai yasan a wani hali yake ciki yanzu." Mommy ta harare shi tare da yin kwafa wato bazaiji ya daina taimakon aljanar nan ba. ya karaso yana cewa "Ya jiki Daddy." ya ce "Alhamdulillah Abdurrahim kamar an zare min ciwon haka naji, kirjin ne dai ke min zafi har yanzu." "Insha'allahu shima zai daina." bai bar d'akin ba sai da ya bashi wasu allurai da magunguna. Umma Karima ta rasa ina zata sa kanta, tarika dibi-dibi tayi nan tayi can daga karshe tasa direban ta ya jata zuwa dajin Mali. tana shiga kogon boka Mali ta ganshi zaune yana ta aikin zuba tsafe-tsafe da surkullensa. ya d'ago da jajayen manyan idanunsa masu muni cikin murya maraddad'i ya ke fad'in "Wace ce ita da muka kasa ganin ta a zahiri kamar yadda muke ganin duk wanda muka kira shi cikin wannan kwaryar!? akwai wani abu a tare da ita mene ne shi, mene ne shi na kasa ganin shi!!." Umma Karima ta zabura ta zube gaban sa tana fad'in "Boka a gafarce ni, wannan yarinyar ta zame min karfen kafa na rasa ta in da zanbi na yakace ta a wannan gida, duk wani makircin da zan gina mata sai ta sallaka, yau ana daf da idda cin nasara tafi to tana shirin lalata nasarar, yanzu haka boka nasashi ya tattaro duka takardun kadarorinshi, yau nake shirin sashi ya juya sunan ya dawo nawa, da zaran ka bashi maganin cikin kwaryar nan, shine shegiyar yarinyar nan ta fasa kwaryar, boka a taimaka a kuma d'aukar wata kwaryar muje a bashi maganin." boka Mali ya kece da dariya "Hahahaha kin rigada kin tafka asara, aiki ya wargaje, je ki leka cikin tukunyar tsafi ki gani." jiki na b'ari Umma Karima ta mike ta je ta leka tukunyar tsafin. kirji ta buga ta waro ido cikin tukunyar, da kullum ke tafasa yau babu ko alamar d'igon abu a ciki, hasali ma tukunyar a bushe take kamas kamar tun da yake ba a ta ba'a amfani da shi ba. ta juyo gareshi hankali a mugun ta she ta ce "Boka babu komai cikin tukunyar ina abun ciki suke?." "Hahahaha a gidan ki kwarya ta fashe fashewar kwarya kuma yana dai-dai da rasa abun da suke cikin tukunya, shi kansa tukunyar a fashe yake kece bazaki gani ba, do le sai kin kuma samo wasu a had'e guri guda masu kwari a saka cikin tukunyar, kafi aikin ki ya farfad'o a ci gaba." jikin Umma Karima ya tsanan ta rawa murya a daburce ta ke fad'in "Boka kasan da ya na samo wannan na karshen, shekara nawa nayi ina nema kafin na samu, daya na samo wannan d'in ma, wannan tsinanniyar yarinyar tayi ajalin abin da na jima ina nima wlh bazan kyale ta ba, yadda ta rushe min mafarkina sai na hanata ko da dai-dai da rumtsawa ne, yanzu boka ai ki ya tsaya ke nan?." "Ai ki ya tsaya da alamun faruwar wani lamari, ki gaggauta nimo lakanin ki a sake gina miki aikin ki." Umma Karima ta mike a haukace tayi waje tana tsinewa Feeryal.. A b'angaren Dad ba karamin girgiza ya yi da ganin Daddy ya farfado ya dawo hayyacin sa ba. shi da yake ta kan shirin yadda zaiyi ya kwashi dukiyar sa duka, ya barshi cikin latauci da jinya. ya ciza yatsa yana buga teburin gaban sa. "Ban so haka ba amma zamu had'u next time ni zanyi nasara, sai ka d'and'ana bakin cikin da kuka jefani ciki kai da mahaifiyar ku, sai na fanshi dukiyan mahaifina da aka yi rufarufa akace duk mallakin ka ne, daga karshe na fanshe ran mahaifiyata da taku mahaifiyar." ya mike ya rufe office d'in sa ya nufo gida. Gaba d'aya gidan tun daga kan 'yan gida da ma'aikatan gidan kowa murnar samin saukin Daddy ake. in a ka cire Umma Karima da Dad Mom. farincikin da Aunty ta ke ciki bazai fad'u ba. tana nan a nanike da shi. Kwana uku da farfad'o war Daddy yana zaune a bedroom d'in sa, gaba d'aya ya nisa cikin tunani tun ranar da ya dawo hayyacin sa, yake ta tunanin mafarke-mafarken da yarikayi abun da yafi tsayuwa masa arai shine hasken da yake zuwa ceton sa. da maganar da ake masa kan hasken. da kuma fuskar da ya gani daga karshe, abun da ya d'au re masa kai. me yasa ake cewa karya bari ta tsere daga raguwar sa, ta zauna cikin rayuwar sa. bayan a cikin gidan sa take tamkar d'iyar da ya haifa, yakan mance da ba shine ya haife ta ba har sai in magoratan gidan sa sun goranta. wani irin kusanci ne ake nufi daya yawuce wannan, gashi ana gaya masa zai kuma shiga wani tarkon nan gaba, idan baiyi gaggawar kusanto ta cikin rayuwar sa ba. sosai kwakwalwarsa ta hargitse da tunani ire-ire.......! Mommyn Twins ce 25 Umma Karima zaune a parkour'n ta ita da iyalan ta, abin duniya duk ya taru ya dame ta. shike nan duk bojet d'in ta ya rushe da yanzu ba wannan maganar akeba, da yanzu bata ma kasar ta milla wata kasar. tsaki ta ja akararo na sau ba adadi. Nabila dake danne-danne a wayarta ta d'ago tana fad'in "Kai wai dama wannan duk gidajen Daddy ne da suke Abuja, ai da ya rasu ni cikin wad'an nan gidagen za'a bani da suke Abujan nan." Bilkisu Saddiqa Rahma suka d'ago a tare Bilkisu ta ce "Amma Nabila baki da hankali Nabila yanzu har tunanin Daddy ya mutu dan ki sami gidaje kike, duk cikin mu babu wan da ya tab'a wannan tunanin sai ke ai ki gansa a raye yafi miki wad'an nan gidajen." Nabila ta mike ta nufi bedroom d'in su tana fad'in "Mutuwa ai wajibi komai daran dad'ewa ai dama zai mutu." "To sai ki bari lokacin nasa ya yi tukun." cewar Saddiqa. Umma Karima ta ce "Kai dalla ku rabu da ita haka, in da ku d'in ne ma hakan zakuyi idan ya mutu sai kunji kuna son wasu gidajen fiye da wasu, haba dan Allah ku barni naji da abin da ke damu na." Rahma ta ce "Umma ai dai bai mutun ba tukun meye na maganar nata, Umma wai me ke damin ki ne kam?." Umma Karima ta girgiza kai kawai tana jin kamar ta mutu dan bakinciki. Siyama ta fito tana gyara mayafi ta dubi Umma Karima tana fad'in "To Aunty Karima ni bari na fita nayi bako a waje." Umma Karima ta d'ago ta kalleta sama da kasa wasu d'amammun kaya ne a jikin ta. ta ce "Wai ni wane ne kika samu ne me zuwa babu dare babu ranar nan, kuma ya d'auke ki kuna fita?." fuska ta yamutsa ta ce "Kawai hirar rage zafi ne kafin wancan ya shigo hanu, d'an fita zamuyi yanzu zamu dawo." Umma Karima ta juya kai bata kuma cewa komai ba tacigaba da tunane-tunanen niman mafitan ta... Aunty ce zaune cikin bedroom d'in ta rike da waya a kunnen suna magana da Hajja Umma. daga cikin wayar Hajja Umma ta ke fad'in "Ikon Allah kuma tana bacci tasan wani mai magani ya shigo gidan, kinsan masu jinnu irin haka a kusa basa son marasa gaskiya, gidan nan naku akwai wani abu ke dai kar ki yada addu'a babu abin da ya fi karfin Allah, amma yanzu ya jikin Alhajin babu komai dai ko." "Jikin sa da sauki sosai mafarkan ma duk ya daina, sai dai kirjin da yaje kukan sa dama shi tuntuni Abdurrahim ya d'aura shi a kan magani." "To Allah ubangiji ya dad'a yaye masa, dama Abban ku najiran yasa mi lafiya ne, ya same shi da batun wannan yaro Sadam iyayen sa sun zo nima masa auren Feeryal ya ce sujira yasami uban ta idan sukayi magana ya amince sai ya turo su nan Lagas d'in, to yaron wai shi a sonshi a had'a auren shi da abokin sa Nasir, Abban ku ya fad'a musu yanzu zata fara karatu matsalar da aka samu da 'yan tawagar d'aukar amaryar nan ne ya tsaida batun tafiya makarantar ta, sun ce babu damuwa idan akayi auren sai ta cigaba da karatun ta, sau biyu fa suna zuwa, ban da shi yaron da yazo yafi a kirga." Aunty ta ce "Hajja Umma da wurwuri haka bikin Maryam da saura wata d'aya, a dai bari idan aka yi natan sai ayi na Feeryal d'in daga baya, ni nafi so Feeryal ta kara girma tafi haka kafin tayi aure." Hajja Umma ta ce "Fatima a wannan hali da ake ciki na ko da yaushe samari suna kawo mata hari dan ma Allah yana ketar da ita, ai a aurar da ita shi yafi miki rufin asiri ke kan ki sai kin fi samin kwanciyar hankali, imma baza'a had'a bikin dana Maryam ba bayan bikin ayi natan kawai ya wuce, tun da bikin Maryam d'in yazo daf, taje ta cigaba da karatun ta tana da aure ai yafi." Aunty ta sauke numfashi tabbas idan ta aurar da ita zatafi samin nutsuwa da kwanciyar hankali. kullum tana cikin fargabar yawan kai mata hari da maza keyi. ta ce "To shike nan Hajja Umma zan fara samin Daddy da batun kafin Abban ya kirashi in yaso daga baya iyayen Sadam d'in suzo." sukayi sallama ta kashe wayar. Siyama bata dawo gidan ba sai da yamma lis saurayin nata ya dawo da ita. yana sauke ta a mota Saddiqa na fito wa. ya zuge glass d'in motar suka had'a ido ya sakar mata murmushi, itama ta mayar masa. ya leko yana fad'in "Wannan fa naga kunyi kama da ita." ya yi maganar yana maida kallon sa kan Siyama. Siyama tawani narke murya tana yauki ta ce "Saddiqa wai d'iyar Aunty ta ce, ai dole muyi kama." Saddiqa ta karaso gurin ta dube shi da murmushi ta na cewa "Inayini Uncle." ido d'aya ya kashe mata sannan ya amsa gaisuwar nata. Siyama ta dube shi tana fad'in "Baby sai yaushe?." "In kin so ko anjima da daddare sai na dawo." "Ah ka bari sai gobe." "To Allah ya kai mu." ya dubi Saddiqa ya ce "To sai anjima 'yanmata." hannu ta d'aga masa ta ce "Mu kwana lafiya." ya ja motar sa ya yi gaba, su kuma suka shige ciki Saddiqa tana cewa "Aunty Simaya a ina kika samo wannan amma fa ya had'u." Siyama ta washe baki ta ce "Ba kad'an ba fa bamu jima da had'uwa da shi ba, kinga har maganar aure yake min, amma duk had'uwar shi ai bai kai yayan ku ba, badun ina da sammanin samun Abdurrahim ba da wannan zan aura." Saddiqa tayi dariya suna shigewa parlour'n su. Da daddare Siyama na kwance suna waya da saurayin nata, cikin hirar tasu yake tambayar ta ina mai kama da ita. ta ce "Tana can d'akin ta." ya ce "Allah kuna kama fa sosai kyakkyawa kamar ki." Siyama ta washe baki dajin dad'in an yabe ta an ce mata tana da kyau. ta ce "Ai haka kowa yake fad'a muna kama da ita, d'azu ai itama sai da ta tambaye ni wai a ina na samo had'ad'd'en gayen nan." dariya ya sake yana fad'in "Au ki ce ita ma ta tambaye ni kamar yadda na tambaye ta yanzu." "Eh wlh tayi maganar ka d'azu ma, ko na kaimata ku gaisa ne?." "Aa ki barta dare ya yi kidai bani number ta ma gaisa ko ta Whatsapp ne, mai kama da baby na kyakkyawa." Siyama tayi dariyar jin dad'i, ta ce "Tom zan turo maka." suna gama wayar ta tura mishi lambar Saddiqa. Koda Aunty ta sami Daddy da batun da Hajja Umma tayi mata kan Major Sadam, yanzu ya matsa yana so inda so shine samu a had'a bikin su dana abokin sa Inspector Nasir. Daddy ya yi shuru sannan ya ce ace su dakata tukun ba yanzu ba... Kullum Umma Karima a cikin tunani take na yadda zata bi ta idda samin nasara a karo na gaba ta ke. har in tana bukatar samin nasara kuwa ya zama dole Feeryal tabar gidan, ta nan ne kad'ai idan tayi jifan ta zai fad'o kan wanda take so batare da an tsare shi ba. sai dai wannan karo tana bukatar taimako dan ta lura a yanzu dole sai ta sami mai tallafa mata kafin ta idda kudirin ta. da sauri ta mike ta d'au mayafi tayi sashin Mommy. a parlour ta tadda Mommy ita da su Ameerah. Mommy na ganin ta tasan wani labarin ta kawo mata, ta jata sukayi cikin d'aki. a bakin gado duk suka zauna, Mommy ta dubeta ta ce "Ya dai Hajiya Karima akwai labari ke nan." Umma Karima ta gyara zama cikin dabara da kwarewa a iya makirci take fad'in "Yanzu Hajiya Halima haka zamu zuba ido mucigaba da kallon matar nan, da wannan aljanar ruwan da ta kawo mana ita gida, ta zame mana fitina alakakai, to bari kiji ina mai maganin da na kawo shi rannan ya duba Alhajin nan, ya ce yarinyar ba karamar matsafiya bace, aiki tayi da tsafin ta har ta kore shi a gidan, yanzu haka ya ce idan bamusan yadda mukayi muka fitar da ita a cikin gidan nan ba,to wlh mu sai ta fidda mu kaf a kan 'ya'yan mu." Mommy ta dafe kirji ta ce "To yanzu meye mafita Hajiya Karima, wannan hasabibiyar yarinyar ya zamuyi da ita?." "Mafita d'aya mud'agawa Alhaji hankali mu tada bori cikin gidan nan, mu zuga Hajiya musa ta tasa shi ya kore ta, in ba haka ba fa ina mai tabbatar miki muzata kora cikin gidan nan, kuma duk shirin Hajiya Fatima ce makirarriya ta kwantar da kai ta had'a mu da gamasheka, tana sarar mu ta kasa." Mommy ta ce "Amma fa Hajiya Karima idan muka ce zamu d'aga hankali da yawa kinsan halin Alhaji karshe ya ce, zamuyi a bakin auren mu, ni kinsan fa saura biyu ne sakanin mu ya guntule d'ayan tuntuni, gara ke ma bai tab'a yi mi ko d'aya ba, ni ina ganin kawai mubi a sannu mu sami Hajiya mu tuna mata ai dama ya ce, idan aka gama bincike ne akan wanda suka sace ta mai tawagar d'aukar amaryar nan, zata koma can Abuja, mu tuna mata da wannan batun dan naga kwana biyu tayi shiru, kuma nasan har da ciwon Alhajin ne ma yasa tayin shiru, tun da ya sami sauki zance ya kare tasashi ya koreta ta koma can in da akayi gayyar ta." Umma Karima ta d'anyi shiru bataso haka ba, taso Mommy ta d'auki zugarta kamar yanda kullum take sata akan keken b'era. ta ce "To shikenan hakan ma za'a sami nasara, bari zan sami Hajiyar nasan yadda za'ayi." nan ta cigaba da kisawa Mommy yadda zasuyi kafin ta koma sashin ta... Shirye-shiryen bikin Maryam da Inspector Nasir yana ta matsowa, duk abun da aka sawa rana komi daren dad'ewa zai iso. ana saura sati d'aya bikin Aunty da Feeryal suna zaune a parlour kiran Maryam video call ya shigo wayar Aunty. Aunty na d'agawa Maryam ta turo baki tana fad'in "Aunty Faty wai sai yaushe ne zaku zo ne kam, biki saura sati d'aya ai yau ya kamata kuzo." Aunty ta ce "To mara kunyar amarya mai kiran a zo bikin ta." dariya duk sukayi Feeryal na dariya ta ce "Aunty Maryam an gama d'inkamin ashobe na kuwa?." "Ke da Sadam yazo ya karb'i naki wai zai kai da kansa a d'inka miki, jiya ma suna nan yayi ta kiran wayar ki baki d'aga ba." shiru Feeryal tayi sarai taga kiran shi jiya, bata d'auka ba, yau da safe ma sai da ya mata missed call yakai biyar bata d'aga ba. maganar Maryam taji tana fad'in "Ai bakiga d'inkin da yasa akayi miki ba ya nuna min hoton su a waya." murmushi kawai tayi tana kwantar da kanta a kafad'ar Aunty. Aunty ta bita da ido tana son karantar yanayin ta. "Aunty Faty dan Allah ku taso gobe." Maryam tayi maganar tana marairaice murya. Aunty ta ce "Sai ana gobe d'aurin aure zan shigo, ni kad'ai Daddy ya ce zan zo banda Feeryal, ya ce har yanzu ba'a gama bincike ba, shigowarta Abuja yana da hasari yanzu." da sauri Feeryal ta d'ago murya kamar zatayi kuka ta ce "Ayya Ammie ni dai zanje." "Aa Feeryal ki bari tukun komai yagama dai-dai ta, idan natafi ana gobe kwana biyu kawai zanyi na dawo." "Ayya yanzu Aunty Faty banda ita ke nan a zuwa, wlh ni har naji auren ma yafita min a rai." Maryam ta fad'a kamar itama zatayi kuka. Aunty ta kashe wayar ganin duk suna son caza mata kwakwalwa. Feeryal har da kuka ita ala dole sai ta bita. da kyar Aunty tayi ta rarrashi har sai da Daddy ya shigo ya taya ta. ya ce tayi hakuri itama zataje saura kiris a kammala bincike... Ana goge d'aurin auren kuwa, Aunty ta gama shirinta tsaf zatabi jirgin karfe 9 na safiya. yau Feeryal ko baccin safiya bata koma ba, tana nan tana bori ita sai tabi Ammie'n ta. tun a daren jiya Miemie tazo ta kwashi wasu kayan ta tana ta murna dan a sashin su zata zauna kafin Aunty ta dawo. ai kuwa da sassafe ta zo side d'in Aunty. karfe 8 dai-dai Daddy ya ce Aunty ta fita direba ya kai ta saboda karfe 9 jirginsu zata d'aga. a tare suka fito Feeryal kayan bacci ne a jikinta ta d'aura hijabi iya gwuiwa a kan kayan baccin, tana tafiya tana sharar kwalla. Miemie na d'auke da d'an madaidaicin akwatin Aunty. a can tsakiyar farfajiyar gidan mota ke jiran ta. Daddy na zaune a bayan motar Abdurrahim na tsaye a jikin kofar gefen da Daddy yake. tun kafin su karaso direba ya yi saurin bud'e wa Aunty d'aya gefen, suka karaso Aunty na kokarin shiga motar Feeryal ta saki kukan shagwab'a tana bubbuga kafa kasa tare da yarfe hannayen ta, cikin muryar ta mai sanyi take fad'in "Ammie ni dai zan biki." Daddy ya ce "Aa Feeryal ina mun gama wannan maganar tun jiya, kiyi hakuri idan komai ya dai-dai zakije ai, yanzu kam babu halin ki shiga Abuja gaskiya, kiyi hakuri kinji." bayan hannun ta takai tana share hawaye tana jan shashsheka, wasu hawayen suna zuba. Ammah da ta karaso gurin yanzu tayi karamar dariya tana fad'in "Aa Feeryal wai duk kukan rabuwa da Ammie'n naki ne haka, to ayi hakuri." Ammah ta dubi Aunty ta ce "Har kun fito ashe to Allah ya kiyaye hanya, a dawo lafiya." Aunty ta amsa da amin-amin. kana Ammah ta d'an rusuna ta gaida Daddy cikin girmamawa. Aunty ta shige mota tana fad'in "Yanmatan Ammie kwana uku fa kawai zanyi na dawo, a daina wannan kukan dan Allah." Feeryal hanci takuma ja tana goge ido da bayan hannu. direba ya yi wa motar ke Daddy ya dubi Abdurrahim yana cewa "Ka duba yuwuwar dacewar sayar masa da duka gonakin audugar 30 wad'an da ba'a sasu a jadawalin kai su company ba, na gaya masa kai ba manomi bane likita ne bansan me yasa yake son sako ka cikin lamarin ba, ko da yake ya ce min wai kafini sanin harkar noma, na ce wane kai tun kan a haife ka nake noma, in ya ce fed'e mutane a d'inke to na yadda." murmushin gefen baki ya yi tare da rufe masa murfin gefen sa. Aunty ta gyara zama tana fad'in "Daddy ka had'a kanka da shi shifa d'an zamani ne." cikin yin kasa da murya Daddy ya ce "To bayan ina da ke 'yar zamani ai nima nazama d'an zamanin ke nan." murmushi ta yi shima ya mayar mata. kana yacewa direba yaja su tafi, dan shi zai rakata airport d'in da kansa. Feeryal takuma yin rau-rau da ido sai ga hawaye sharr san da taga motar su Aunty yana shirin fita daga gidan. Amma ta ce "Taho muje Feeryal yi hakuri mana kinji, kin san matsalar da yasa baza'aje da ke ba, badun son kare ki daga 'yan ta'addan can ba ai da dake za'aje." Ammah ta yi gaba. Miemie ta ruko hannunta ta ce "Muje Feeryal." a hankali ta soma d'aga kafarta tana waigen baya in da take hango fitar motar su Aunty. gajeren tsaki yaja idanunsa a kan waya. zura wayar dake rike a hannun nasa ya yi cikin aljuhun jallabiyar jikin sa. kana ya zura hannayensa duka cikin aljuhun, har suka zo daf da shi zasu gotashi Feeryal bata fasa waigen ba. ya saka mata kafa ta fad'i tim a kasa. kara ta sake tare da fad'in "Wayyo Ammie na, wayyo kafata." ta rike gwuiwa tana yarfe hannu kwalla na zuba. da sauri Miemie ta sunkuya tana yi mata sannu dan bata lura da abin da ke faruwa ba. Ammah ta juyo da sauri ta dawo in da suke tana fad'in "Sannu Feeryal fad'uwa kikayi ne garin yaya?." shiko gefe yabi ya wuce cikin garden ya yi zamansa. Ammah da Miemie suka tallafo ta suwa sashin su tana tafiya tana yarfe hannu... Kwanan Aunty biyu a ran na uku ta juyo dan hankalin ta na gida gun Feeryal, duk da tasan Ammah zata kula mata da ita. Siyama ce ta fito daga d'aki ta wuce dinning ta bud'e kular abinci zata d'iba. da sauri ta toshe hancinta ta juya da gudu ta koma d'aki, ta wuce bayi tashiga kela amai. Umma Karima da ke zaune a parlour ta bi bayanta da kallo. zuwa can ta fito tana yamutsa fuska. Umma Karima ta ce "Ya dai Siyama me ya faru kamar amai naji kike yi?." fuska ta dad'a yamusawa ta ce "Wannan matar Sukai na ce ta dai na cika wad'an na Spices d'in cikin abinci amma bataji ba, wari suke min da zaran na zo ci sai naji zuciya ta na shi." ido Umma Karima ta ware ta ce "Siyama kar dai zargina ya kasance gaskiya, gaba d'aya yanayin ki ya koma irin na masu ciki,kwana biyun nan." kame-kame ta shiga yi tana fad'in "Ci..ci...ciki kuma Aunty Karima a'a kam ni kam bani da komai." Umma Karima ta mike zumbur ta ce "Haba Siyama nasan jiya fa nasan yau, to me zaki b'oye min ma tukun, wani irin hauka ne ya kaiki barin ciki ya shige ki, wannan d'an iskan dake zuwa babu dare babu narar nan shine ya miki ko?, na shiga uku ni Karima zaki lika mana abun fad'a." da sauri ta d'au wayarta ta kira lambar Family Dr su, yana d'agawa ta ce "Duk abin da kake kabari ka zo, ina niman ka." ya ce "Kiyi hakuri Hajiya wlh bana ma garin nayi tafi sai jibi zan dawo." Umma Karima ta kashe wayar da sauri bata jira ya gama maganar nashi ba. ta ce "D'auko mayafin ki da sauri kizo muje, yau cikin nan bazai kwana a jikin ki ba, kafin wani ya ankara an cire d'an banza, ina zan iya ina fama da wani damuwar wani damuwar ya kuma kunno kai, akwai wani arnen likita gurin shi yanzu zamuje yanzu ba sai anjima ba." ta shige d'aki da sauri itama ta d'au mayafin ta suka fito. tun kafin su karaso parking lot take kwad'awa direba kira, ta ce ya taho da makullin mota da sauri. suka shige mota tayi masa kwatancen asibitin da zai kaisu, wani private hospital ne. suna isa ta janyo ta da sauri sukayi cikin asibitin. bayan an bud'e musu Folder aka turasu ofishin likita. suna zama Umma Karima ta soma kora masa bayani jiki na rawa, ta ce ko nawa ne ita zata biya bata so cikin ya kwana a jikin ta. ya caja su 500k batare da b'ata lokaci ba tayi masa transfer zuwa account d'in sa. kud'in suna shigo masa ya mike ya ce yana zuwa. ya fita. Abdurrahim na zaune cikin office d'in sa sako ya shigo wayar sa. ko da ya d'auka ya bud'e, hoton Umma Karima da Siyama ya gani. yana kokarin aje wayar kira ya shigo. sunan Dr L-cana ya bayyan a screen d'in wayarsa. kamar bazai d'aga ba har wayar takusa yankewa kafin ya d'aga. daga cikin wayar Dr L-cana ya ce "Hello AA How far, how you are there." ya ce "Fine." Dr L-cana cikin harshen sa da bai gama sayawa ba ya ce "Wannan kamar matar Daddy'n ka ne na gane fuskarta, d'ayan ce dai ban gane ta ba sai dai naga sunyi kama ko daughter ta ce, abortion suka zo ayi wa yarinyar, nayi wani tunani nace bari na sanar maka, kar azo a sami damuwa, shin nayi mata?." a zafafe ya ce "Then, So what! meye nawa da zaka kirani kana gaya min, It is not my.concerned, I don't have problem, damuwar su ce wannan, so please Don't call me again; ko ma meye ku kara ta." ya kashe wayarsa yana jan dogon tsaki.........! Mommy'n Twins ce Ganin ya kashe wayar Dr L-cana ya d'aga kafad'a tun da ya yi ko oho da maganar shiko yana ganin kud'i bazai barsu ba, komai ya faru ma daga baya ne. ya koma ciki yasata ta tube ta haye gado. ya had'o kayan aikin sa batare da b'ata lokaci ba ya burge cikin. ya bata magunguna suka nufo gida. suna isa gida Umma Karima ta jata d'aki ta sunkiya mata bala'i. "So kike ki samu a bakin mutanen gidan nan, badun na ankara da wuri ba ai da zance ya kwab'e, idan mutane suka sani har ya shiga kunnen Abdurrahim ai shike nan kuma, sai mun nimi yadda zamuyi mu rufa bakin sa, kar ki kara irin wannan ganganci; ki cigaba da shan magani ki warke ko su Bilkisu kar ki bari su gane komai." tayi waje tana janyo mata kofar. A b'angaren Abdurrahim bakin cikin kiran da Dr L-cana ya yi masa akan Siyama da Umma Karima, an danganta shi da su da abun bakin cikin da sukaje yi yaji, ya tattari abubuwan amfanin sa yazari makullin motar sa yabar asibitin. yana isa gida ya gyra parking yafito ya nufi side d'in sa. direct upstairs bedroom d'in sa ya nufa. yana tura kofar yaja ya tsaya cike da mamaki yaji b'acin ransa ya karo. masu aiki yagani guda biyu cikin d'akin, d'aya tana d'ale a kan gadon sa tana gyarawa d'ayan kuma tana cikin bathroom d'in sa tana wankewa. wani uban tsaya ya buga musu, a razane duk suka taho gaban sa suka zube. cikin muryar b'acin rai sosai ya ce "Waya baku damar shigo min side d'ina har ku wuce ko ina ku shigo min har cikin bedroom!?." murya na rawa suka ce "Mai d'akin ka ce Hajiya Kuraiba." wani b'acin ran yakuma jin ya ziyarce sa. cikin tsawa ya ce "Ku fita ku b'ace min da gani! ko da wasa na sake ganin wata ta sako kafarta cikin side d'in nan ba ma d'akin nan ba, wlh sai kun raina kanku." a zabure sukayi waje jiki na kyarma. a stairs sukayi kiliya da Kuraiba da taji dawowarsa ta shigo gefen sa. ganin yadda suke sauka kamar ana biyo su ta ce "Kai wai har kun gama gyaran ko ya?." basu iya bata amsaba sukayi waje da gudu." da sauri ta karasa haurawa tana shiga ta gansa yana tsaye yana rage kayan jikin sa, fuskarsa babu annuri. ta karaso tana kokarin rungume sa ya buga mata tsawa tare da nunata da yatsa murya cike da b'acin rai ya ce "Waya baki ikon shigo min da wad'an can abin cikin d'aki, ke kanki albarkacin Mommy kike ci, badun haka ba na rantse baki isa ki taka kafarki cikin bedroom d'in nan ba, gargad'i na karshe, kada ki sake ki sake gayyato min wasu 'yan'aiki cikin side d'innan ma gaba d'aya." duk da taji tsoron yadda yake magana cikin fusata sosai, amma sai ta waske cike da salon bariki ta narke murya "Haba mijin Kuraiba ai yanzu ni nake da ikon sawa ko hanawa a cikin gida na, wai kullun ina gidan amma wai sai Ajmaal ya shigo ya gyara maka bedroom's zuwa parlour, shine yau na ce yabari ni zan sa masu aiki su gyara idan sun gama gyaran nawa." wani irin mari ya d'auke ta dashi tun kan ta kaiga rufe bakin ta. cikin karaji ya ce "Bakiji me nace bane!? masu aikin ne bana so su tab'a komai nawa, idan kika sake gigin gayyato su nan wallahi! sai kin raina kanki, akwai kofa ta can sakanin inda kike da waje ki bud'e surika shigo miki ta can, ban yadda na gansu a area'n nan ba! fita a d'akin nan yanzun nan!!." yakuma buga mata tsawa, ta juyo da sauri dafe da fuska tayi waje tana fad'in "Ka mare ni Abdurrahim." tsaki yaja ya shige bathroom. Yana fita ya tarar da Missed call d'in Mommy a wayar sa. yana saka kaya ya fita ya tafi sashin Hajiya. Hajiya na ganin sa ta ce "Yauwa abikin turawa da ma yanzu nake kan cewa Kulu ta kira min kai, ciwon gwuiwan nan ya sako ni gaba kwana biyu." zama ya yi yana fad'in "Muga kafar." ta ja zani saman gwuiwar tana cewa "Ka ganshi nan zugi kamar ya kwana biyu hanani bacci yake, yanzu ko na sha na shafa maganin da ka banin nan baya dai na zugin." yatsar sa ya d'aura kan gwuiwar yana d'an daddannashi sannan ya d'ago ya gyara zaman sa ya ce "Za'a canza miki magani, anjima zan kawo miki." "Yauwa ai gara a kawo min wani, wannan gwuiwa ya sako ni gaba." bai kuma magana ba sai wayarsa daya zaro yana daddannawa. Hajiya ta gyara zama ta dube shi tana rike hab'a tare da fad'in "Wai ni kam abokin turawa har yanzu banji ana fad'in yarinyar nan Kuraiba ta d'auki ciki ba, ko baku fad'a bane? to ai ko baku fad'a bama za'aga alamar ciki tare da ita, akwai cikin kuwa?." baki ya tab'e batare da ya ce komai ba. Hajiya ta ce "Ni halina da kai ke nan, ana ma magana kayi banza da mutane, gara ka fad'a tun da wuri a sani a nemo maganin tsari a sunkuya bata, dan gidan nan yanzu ya zama abun da ya zama miyagu suna son kafa sansanin su, ban san me ke damin Abubakar ba wannan yarinyar Feeryal ba abin a zauna da ita a guri bane, bari zanyi tattaki naje Yelwa na karb'o mata magani a rufa idon makiya akan abun cikin, idan ta bar gidan ba shike nan ba kowa ma ya huta, wannan karo ko ba'a gama bincike ba zata koma, iya shegen banza kawai ina gashi nan ni ina ganin ku ina jin dad'i, shine bazai so ganin jikokin sa ba, idan aka barta tayi wa cikin wani abu fa tun da su dama jinnu sunfi son karnin jini, kafin a sake samin wani ai sai an kuma yin wani watannin, ba gara a tare ko mai tun da wuri ba, bari Abubakar zai zo ya same ni." d'ago idon sa ya yi daga kallon waya ya kalle, wato ita a lissafin ta ciki Kuraiba take da shi. baki ya tab'e ya mike yana fad'in "Da ma tana da ciki ne?." "Yo iyashegen banza ai kai kafi kowa sani in tana da shi ko babu, kardai kuyi irin abun zamanin nan aure kusan wata 6 ai yaci ace yanzu tana da cikin wata 5 ko shidan ma." takalmansa ya zura ya fice daga nan ya wuce masallaci... Bayan wata biyu da cire cikin Siyama Bilkisu da Saddiqa suna zaune a d'aki wanda dama su biyu d'akin su d'aya, Rahma da Nabila suma d'akin su d'aya, Siyama nata daban. Saddiqa da yawu ya cika mata baki ta mike taje ta zubar a toilet ta dawo. jim kad'an ta kuma zuwa ta zubar. ta kuma mikewa zataje zubarwa Bilkisu ta ce "Ke dalla kin dami mutane da tofe-tofen yawu, wai ba dama mutum ya zauna kusa da ke sai yawu, wani iskancin saran da kika samu kwana biyun nan ke nan, kibi ki ishi mutane da yawu da kakarin amai." Bilkisu bata rufa baki ba Saddiqa ta kuma mike wa da gudu ta shige toilet tashiga kakarin amai. Bilkisu ta mike tsaye ta taho bakin kofar toilet d'in ta ce "Ke Saddiqa wai me ke damin ki, baki da lafiya ne bazaki fad'a a kira Family Dr ya zo ya duba ki, ko kije ki gayawa Ya Abdurrahim ya baki magani ba." Saddiqa ta mike tana kuma tofar da yawu. Bilkisu ta harare ta tana kuma fad'in "Wlh ni ni yanzu bamma yadda da ke ba, jiya maganar me kike sakan dare a waya, duk da a bacci na tashi amma na fahimci akwai wani abun da kike b'oyewa." ta juya da sauri tafita a d'akin ta nufi d'akin Umma Karima tana shiga ta ce "Wallahi Umma ban yadda da Saddiqa ba, ki kirata ki binciketa wlh kamar ciki take da shi, tabi ta dame ni da amai da zubda miyau." Umma Karima ta zabura tare da buga kirji ta ce "Ciki! nashiga uku ina Saddiqa'n ta ke." ta mike a haukace tayi waje tana kwad'awa Saddiqa kira. Saddiqa ta fito da sauri jiki a sanyaye. Umma Karima ta dubeta sama da kasa tana haki sannan ta ce "Biyo ni nan maza ki bani fitsarin ki na gwada in dai ciki ne kin gama da ni Saddiqa." Bilkisu Rahma Nabila Siyama duk suka rufa musu baya. Kulu mai aikin Hajiya da tazo karb'awa Hajiya hayaki gun Umma Karima, taja ta tsaya tare da rike baki tana binsu da kallo har suka shige d'akin Umma Karima. Umma Karima ta d'auko tsinken gwajin ciki ta mika mata d'an karamin kwantena ta sata gaba suka shiga bayi tana tsaye a kanta tayi fitsari ta bata. ta saka PT ciki taja ta tsaya tana fifita da d'an kwalinta. bai mata ba ta fito parlour rike da PT, gani tayi d'akin ya kasa mata. 'ya'yan nata suka biyo ta. wani uban ashar Umma Karima ta mulmulo ganin amsar tana da ciki sinken gwajin ya bayar. ta sake shi a kasa ta sa hannu akai tana fad'in "Nashiga uku ni Karima Saddiqa kema cikin kikayi! a ina kika samo ciki wani d'an kutumar uban ne ya miki ciki!." Kulu ta waro ido ta juya sad'af-sad'af ta yi waje tana kama baki. Saddiqa tayi kasa da kai jiki na rawa. Umma Karima ta buga mata tsawa "Dan uban ki ina tambayarki uban wa yamiki ciki zaki gaya min ne ko sai naci kutumar uban ki." Saddiqa ta zabura murya na rawa ta ce "Um..mu...." sai kuma tayi shiru. Umma Karima tayi kukan kura tayi kanta da sauri ta b'oye bayan Bilkisu tana fad'in "Zan gaya miki Umma." "Zo nan gaba na ki gaya min." ta fad'a tana huci. ta zo jiki na rawa tashiga kame-kame ta na fad'in "Um..um..saurayin Aunty Siyama ne." Siyama da Umma Karima suka waro ido a tare. Umma Karima ta ce "Au tsinanne tambad'ad'd'e, d'an akuya sabo da shi ya zamo bunsuru yabita ya barbare ta yakuma biyoki ke ma, sabo da wancan karon ban d'auki mataki a kan saba, shine bari ya kuma b'ulluwa ta hanyar baya ya d'ura miki ciki ke ma, ke Siyama d'an gidan uban waye ne shi da yake binku yana barbarar ku, sai na ga uban sa Wallahi." su Nabila suka waro ido dan dama basusan da na Siyama ba. Kulu da saurinta ta shige sashin Hajiya. Hajiya na ganin ta babu aikan da ta mata ta ce "Ke Kulu ina hayakin dana aike ki karb'a?." Kulu ta ware ido ta rike hab'a ta ce "Hajiya wlh akwai babban matsala a gidan nan, wannan yarinya Saddiqa 'yar wajen Hajiya Karima ciki take da shi, ciki tayiyo wlh Hajiya yanzun nan aka gano tana da ciki." Hajiya ta saka salati tana fad'in "Wasayyawu ni jikar mutane hud'u Saddiqa'n ce tayiyo ciki, ciki dai acikin gidan nan, maza kirawa min Abubakar da abokin turawa." Kulu ta d'au wayar Hajiya ta kira lambar Daddy yana d'agawa ta mika mata. ta karb'a ta kai kunne tana ta ce "Abubakar kasan musifar dake faruwa agidan nan kuwa, maza kazo yanzu ina niman ka." ta kashe ta ce wa Kulu kira min abokin turawa. wayarsa tayi ta ringing bai d'aga ba. Kulu ta ce "Bai d'aga ba Hajiya." ba'a jima ba Daddy ya shigo da fargabar abin da Hajiya zata ce masa dan yasan maganar Hajiya bazai wuce akan Feeryal ba. tun kafin ya zauna ta ce "Abubakar Saddiqa da cikin shege a cikin gidan nan, wace irin musifa ce wannan, acikin gidan ka cikin shege ya b'ullo." da sauri Daddy da maganar ta duki kirjinsa ya kai hannu ya dafe kirji. ya zauna kan kujera da kyar hannunsa dafe da kirjin sa. "Innalillahi wa innailaihirraji'un!." kalmar data fito daga bakin Daddy ke nan. Abdurrahim da shigowarsa ke nan yaga kiran Hajiya yana masallaci. ya karaso da sauri ganin yanda Daddy ke dafe da kirjinsa zaton sa ciwon sa ne ya tashi yasa Hajiya ta kira sa. ya sunkuya gaban Daddy tare da cire hannunsa dake kirjinsa ya d'aura nasa yana fad'in "Daddy ya kake jin kirjin ya ke maka." ido ya rumtse ya ce "Zafi sosai yake min Abdurrahim." Hajiya ta ce "Yo wad'an nan 'ya'ya su zasu kasheka, bansan meye kake jira ace wad'annan gandan-gandan d'in 'yanmata suna zaune a gida babu aure, ba dole su d'auko magana ba, gaba d'ayan su da an musu aure kan lokaci da yanzu 'ya'ya biyu ko uku suke da shi, har autar tasu Nabila takai ta haifi d'a d'aya zuwa biyu; to Saddiqa ta d'auko ciki sauran ma ba'a san in da hali zaiyi ba." da karfi Abdurrahim ya d'ago ya furta "Ciki!." Hajiya ta ce "Kwarai kuwa cikin shege tayi, wannan irin abin kunya ace daga gidan nan ya fito." wani irin mikewa ya yi damasunsa sukayi wani irin bud'ewa, b'acin rai karara ake iya hangowa kan fuskarsa. da sauri ya juya yana taka kafafunsa a kasa, kasa tana amsa sautin takunsa dip-dip-dip!. ya b'allo reshen fulawa ya nufi sashin Umma Karima. yadda ya fad'o cikin parlour ba 'ya'yan nata ba hatta ita kanta Umma Karima sai da ta razana.. ya yi kan su su Saddiqa da duka kan mai uwa da wabi, ba ita kad'ai ba har da su Bilkisu Rahma Nabila. sai da itacen ta karye tayi kaca-kaca a jikinsu. Siyama ta mike da gudu ta masa bayan Umma Karima dan bulalar sai da ya same ta, ransa ya kai kololuwa wajen b'aci yayi jifa guntuwar itacen hannunsa, ya cafko Saddiqa yana kokarin kuncen belt d'in wandon sa. Umma Karima ta yi saurin cewa "Wlh in gaya maka Abdurrahim fyad'e aka mata, fyad'e d'an iskan yaron ya yi mata bada son ranta ba." wani mari ya d'auketa da shi sai da ta kife kasa. ya shiga nuna su da yatsa cikin kakkausar muya yake fad'in "Wallahi! idan kukasa bakincikin ku ya yi sanadiyyar bugawar zuciyar Daddy, na rantse dukkanin ku sai na cire zuciyoyin ku da hannuna!." ya yi shot da Saddiqa a yadda yake jin kansa idan yacigaba da tsayu zai iya kusan kashe ta da duka......! Mommyn Twins ce Abdulrahim na fita Umma Karima tayi kan 'ya'yan ta tana fad'in "Ai kin gani Saddiqa kin janyo muku duka dukan ku, idan badun nace masa fyad'e akayi miki ba da kinci ubanki a hannunsa, yazama dole kema aje a cire cikin nan, dan wlh ban shiryawa abin kunya ba, 'yan iskan yara suna ni man sa ni a bakin duniya." a b'angaren Daddy kuwa da kyar ya iya mikewa yana jin kirjin sa na yi masa zafi, ya lallab'a ya tafi sashin Aunty. ganin yanayin sa Aunty ta tare shi a d'an tsorace tana fad'in "Subhanallahi ya dai Daddy ba dai jikin ba dai?." ta rike hannunsa ganin yana kokarin zama bakin gado, ya zauna yana mai dad'a kankame hannunta. Aunty tayi kokarin zame hannunta tana fad'in "Daddy bakasha magani ba ko bari na d'auko maka kasha." ya dad'a rike hannunta tare da girgiza mata kai ya ce "Barshi Fad'imatu dan ko na sha ma babu amfanin da zai min." jikin ta ya yi sanyi sosai ta ce "Daddy dan Allah kar ka bani tsoro, me kake ji yanzu, ya kirjin ya ke maka." "Zafi sosai yake min Fad'imatu sai ina ji kamar zafin yafi na baya." kallon sa ta ke cikin tsoro "Fad'imatu." ya kira sunan ta murya a sanyaye ta gyad'a masa kai alamun tana jinsa. hannunta ya dad'a rikewa gam kana ya soma magana "A cikin gida na ni Abubakar Fiya, aka samu mai yin ciki a waje a cikin 'ya'yana, Fad'imatu ina jin zafi sosai cikin zuciya ta." wani irin waro ido Aunty tayi kirjinta ya buga da karfi ta ce "Daddy wacce irin magana ce wannan maraddad'in ji!?." kai ya gyad'a mata ya ce "Tabbas Saddiqa tayi ciki a waje Fad'imatu har haka na gaza a gida na? me mutane zasuce a kaina." Aunty ta dad'a jin gaban ta ya tsinke jikin ta ya yi sanyi matuka, taji rashin dad'in abun ba kad'an ba, duk da mugun hali irin na uwar Saddiqa bazatayi fatan ace d'iyarta ta kasance cikin wannan halin ba, jiki a sanyaye ta ce "Daddy baka gaza ba masu taimako ne aka sami sakaki daga wajen su, uwa ita ke taimakon uba wajen yiwa 'ya'ya tarbiyya, a yayin da uba ya fita nima, kayi hakuri Daddy jarabawa ce babu wanda yafi karfin kaddara, mutane zasu fahimceka dan sun san cewa kai tsayayyen uba ne; ka rungumi kaddara mai imani ne ake jarabtar shi ta ko wacce hanya, shin Daddy ka mance imanin mutum bazai cika ba har sai ya gaskata ya kuma yarda da wad'annan abubuwa guda shida, yadda da ALLAH d'aya ne kayi imani da shi, da mala'ikunsa da duk littattafan da ya saukar, da duk manzannin da ya aiko, da ranar karshe wato ranar kiyama, da KADDARA mai kyau ko mara kyau; Daddy kaddarar mu ce bazamu tab'a ketare masa ba, kayi hakuri dan Allah Daddy ka barwa Allah ko mai kaji Daddy." ta zauna gefen sa ta cigaba da kwantar masa da hankali, wanda cikin kankanin lokaci yaji nutsuwa tare da shi. A cikin gidan kuwa labari ya soma yawo kamar dai yadda idan abu ya faru ake kai kawo da shi. sai dai wannna karo masu yawo da zance kasa-kasa sukeyi dan yau abin maganar daga tushin uwar kai kawo ya fito, wato Umma Karima. tarika sakaye wa tana cewa ai fyad'e aka mata. a ranar da abun ya faru da daddare Umma Karima tasa Saddiqa gaba suka ce sashin Daddy. yana zaune a parlour yana kallon labarai a TV. Mommy na zaune a gefe san yau ita ke da Daddy. Umma Karima ta zauna saman kujerar da ke fuskantar sa, Saddiqa ta zauna a kasa. Umma Karima ta marairaice murya dake nuni da zallar shiga matukar damuwa ta ce "Alhaji yanzu fisabilillahi kaji abin da ya faru, amma baka zo kaji taya hakan ya faru ba, shike nan za'a zuba ido a gyale yaron da ya keta mata haddi ya mata fyad'e ke nan, baza'a d'auki wani mataki ba, ko d'an gidan uban waye baza'a tura hukuma suje su kamo sa ba, shiru za'ayi da batun ke nan abu tun safe kayi shiru bakace ko mai ba har dare." Daddy ya dube ta da d'iyar tata da ta sunkuyar da kai ya jinjina kai tare da fad'in "Me kike so nace a kai bayan ke ce uwan ke ce uban, duk abin da kikaga dai-dai ne kije kiyi Hajiya Karima." daga nan bai kuma cewa komai ba ya kwashi wayoyinsa da system d'in sa ya shige bedroom d'insa. Mommy ta ce "Haba Alhaji bai kamata ka ce haka ba, kamata ya yi ad'au mataki a kan yaron." Umma Karima ta mike cikin d'aga murya take fad'in "Rabu da shi Hajiya Halima, sabo da an gama da kai an wanke an baka, waccen tambad'ad'd'iyar tsintacciyar aljanar ruwan, ganin ta ne ba'ayi ba kawai da daddare kabi ka d'aga hankali ko bacci bakayi ba, alhalin gurin iskancinta ta tafi sai da akaje aka d'auko ta a hotel gurin samarukan iskancinta, sai 'yar da ka haifa wani ya sace ta yaje ya mata fyad'e kayi ko oho, to wlh bazan yadda ba 'ya'yana ba tumakai bane da ko wani d'an iska zai rika hawansu ya share lafiya, zakaga abin da zanyi." ta ja hannun Saddiqa fuuu sukayi sashin Hajiya. suna shiga ta fashe da kuka tana fad'in "Yanzu fisabilillahi Hajiya ace ayiwa yarinyar nan fyad'e, Alhaji ya yi ko oho sai kace zuwa da 'yar nayi gidan nan." Hajiya ta ce "Ke da'alla dakata Karima ki na nufin ki ce da karfi akayi mata cikin, ba maza tabi tayi yo cikin ta ba." Umma Karima tashiga rantse-rantse ta na fad'in "Ga Saddiqa'n ta fad'a da bakin ta ba saceta ya yi yaje yayi mata fyad'e ba." Saddiqa ta kama gyad'a kai tana fad'in da karfi ya yi mata har da kukan ta. Hajiya kuwa ta yadda har tana cewa baza'a kyale yaron ba, kuma zatayiwa abokin turawa magana ya zubar da cikin. Umma Karima ta koma da kwarin gwuiwa ganin hakarta ya cimma ruwa. Washegari da safe kuwa Abdurrahim ya shigo sashin Hajiya da shirin tafiya asibiti. Hajiya ta ce "Yauwa abokin tuwara da ma yanzu nake shirin niman ka, ka d'auki 'yar'uwan ka kuje asibiti ka cire mata cikin nan karya girma ya zame mana abin gori, duk da fyad'e akayi mata amma mutane bazasuyi la'akari da hakan ba, gara tun wuri a cire shi tun kafin a busa masa rai ayi zunubi." wani kallo ya wurgawa Hajiya kana ya juya ya soma tafiya yana fad'in "Ba dai ni ba ba kuma asibiti na ba." ya fice ya shiga mota ya bar gidan. Aunty tashigo sashin Umma Karima ta isketa zaune ita kad'ai sai mai aikin ta da take ta mata hidima. Umma Karima ta bita da kallon mamakin ganin ta yau a sashin ta, wanda tun ranar da aka kawo ta gidan iyayen ta suka kawota sashin Umma Karima tun daga ranar bata tab'a sake taka kafarta cikin sashin nata ba, duk tsawon shekarun nan sai yau. Aunty ta nimi guri ta zauna kan kujera kana ta dubi mai aikin nata ta ce "Bamu guri zamuyi magana." nan da nan ta juya ta bar gurin. Aunty ta gyara zama ta kalli Umma Karima wanda da dama ita ma ita take kallo, Aunty ta yi murmushi sannan ta ce "Hajiya Karima ke nan kina cike da mamakin gani na yau a cikin parlour'n ki zaune a kan kujerar ki ko? aje wannan mamakin ki fiskance ni, kin san me ya kawo ni nazo ne na tuna miki abin da kika manta, yau ga miyagun kalamanki sun fad'a kan d'iyar ki, 'yar da kike kira karuwa ita ta iya tsare kanta da taimakon Allah bata aikata abinda kike ta mata fata ba, sai gashi ke mai tsoron Allah an samo fasa gurbi cikin koyayen ki; na dad'i ina jiran rana mai kamar tayau sabo da na mai da miki amsar kalaman ki, amma kash banso ranar ta kasance rana mai muni irin haka ba, wlh shine Allah nayi bakincikin abin da ya faru, bana farin ciki dan Saddiqa tayi ciki, sabo da itama 'yata ce tun da d'iyar mijina ne, amma ina so ki san da cewa shi Allah sam baya bacci, shi yasa ya nuna miki ishara idan ke mai hankali ce ki gani, kina da wasu 'ya'yan mata rai uku bayan Saddiqa ga kuma kanwarki cikon na biyar d'in su; ki kwanta kiyi nazari kiyi amfani da kwakwalwarki, kiyi kokarin baiwa sauran tarbiyyar da zai sa su kyamaci zina, idan kuma ke kasashshiyar uwa ce, to ki shiryawa goyon 'ya'yan gaba da fatiha, ni da FEERYAL kainuwa ne dashen Allah." Aunty na kaiwa nan ta mike ta nufi kofar fita. Umma Karima ta mulmulo ashar ta auna tana fad'in "Karya kike Hajiya Fatima malamin ki ya yi karya, bai isa ya baki sa'an da zaki shigo min har b'angare na ki nimi ki gaya min magana ba, ni Karima wlh zaki san da ni kikayi, munafukar banza munafukar hofi, ciki kuwa sai dai ki ganshi akan wancan tsintacciyar aljanar ruwan badai akan 'ya'ya na, itama Saddiqa'n ma fyad'e aka mata 'yan gulma 'yan bakin ciki, ba cikin shege taje tayi ba, cikin shege a kanku zai kare." Aunty tayi waje abinta. Umma Karima bata fasa kumfar baki ba. kira ta shiga kwad'awa Saddiqa. Saddiqa ta fito ta ce "D'auko mayafinki kizo muje a burge d'an banza, baza'a haifo shi ya zame min masifa alakakai ba, dama hauka nake na bari a haifo shi." Saddiqa ta koma ta fito da mayafi. sukayi waje Umma Karima bata fasa bala'i ba. Asibitin Dr L'cana suka je ta tura masa kud'i masu yawa, shi kuma ya sunkuya aikin sa. yayi-yayi cikin ya fita abin mamaki ciki yaki fita, shi kansa abin ya bashi mamaki duk kwarewa a iya cire ciki irin nashi, sai ga wannan yana son gagarar sa. kwaya ya cusa mata a gaban ta ya ce suje gida kwayar zaisa cikin yafita dan dole. tun daga hanya Saddiqa ta fara wash-wash, Umma Karima ta ce "Ai dama nakuda zakiyi sai ki daure har ya fita." abu sai gaba-gaba yake har suka iso gida, Saddiqa ta shige d'aki tayi ta birgima. kan kace me tafara fita hayyacin ta, ihun Bilkisu ne yasa Umma Karima tasowa da sauri ta shige d'akin su. ta tadda Saddiqa a sume, tayi ta yayyafa mata ruwa wai ko dan ta farka ina. ba sai ga Umma Karima tana salati da kai kawo cikin d'aki. tayi ta kiran Daddy a waya Daddy bayama gidan yana gun meeting. ta fita a haukace tayi sashin Hajiya tana ihun fad'in Saddiqa zata mutu. suka dawo da Hajiya da ta rud'e ta birkice jikarta zata mutu. Rahma ce tayi ta kiran Daddy da layin ta kafin ya d'aga ta sa kuka tana fad'in "Saddiqa zata mutu." ya ce "Rahma idan lokacin ta ne ya yi Allah ya yafe mata, dama ai shi mutuwa wajibi ne ga kowa." ya kashe wayarsa. Hajiya ta ce wa Nabila da ke kusa da ita "Kira abokin turawa yazo yanzu kar yarinyar nan ta mutu fa." Nabila tayi masa missed call biyar ana shida ya d'aga, ta mikawa Hajiya. a rud'e Hajiya ke fad'in "Abokin tuwa kazo ka ceci ran kanwarka Saddiqa zata mu." d'ip ya kashe wayar sa. Hajiya jin shiru ta ciro wayar baki bud'e. Bilkisu ce tayi tunanin kiran Family Dr su Allah ya yi taimako ba'a dad'e ba kuwa ya iso." da kyar ya samo kanta ta farfad'o tana farkawa kuwa sai ga jini ya b'allo mata. Umma Karima ta sauke wani uban numfashi. Hajiya ta bud'e baki tana fad'in "Yoo cikin ne zai b'are dama yake son tafiya da ita, gara ai da ka b'are da ka zauna ka zame mana abin kwatance cikin dangi." bayan likitan yayi mata duk abin da ya kamata ya tafi, sukuma suka sunkuya gyaran in da jinin ya malala. Bayan dawowar Daddy da daddare Hajiya ta je da kanta ta sanar masa, cikin ya b'are. kai ya girgiza kawai dan yasan Umma Karima ce tayi kalan nata, bawai fita ya yi na Allah ba. Saddiqa wata guda tayi tana jinya zuwa lokacin ta ware ta sami sauki sosai... Daddy ne yafito daga bedroom d'in Aunty da shirin tayiya office, Aunty na biye da shi rike da hular sa. sai da suka zo tsakiyar parlour ya tsaya tare da duban ta. murmushi tayi masa cikin zolaya ta ce "Daddy wai kai bazaka tsufa bane kullum fa a haka kake baka kara gaba." janyo ta ya yi yana kokarin rungume ta tayi saurin gocewa tana dariya da fad'in "Aa Daddy a nan kuma idan Feeryal ta fito fa." murmushi ya yi mata ya kalli kofar Feeryal ya ce "Wannan 'yanmatan taki da alama bacci take har yanzu, a taso ta tayi breakfast." har ya juya zai tafi sai kuma ya kuma juyo wa murya da alamar shiga yanayin sanyin jiki ya ce "Fad'imatu idan na dawo akwai wata maganar da nake so muyi da ke, amma kafin nan zan tinkari Hajiya duk da zuciyana yana bugu da sauri-sauri, har ina jin yana min zafi, amma zan tinkare ta ahakan duk da bani da tabbacin samin nasara." Aunty ta dubeshi cikin rauni ta ce "Daddy mene ne kuma." murmushi ya yi mata ganin nan da nan ta shiga damuwa ya ce "Babu ko mai sai na dawo ai nace zamuyi magana ko, kiyi min addu'ar samin nasara, a gurin Hajiya." kai ta jinjina. har gurin mota tarakashi sannan ta mika masa hularsa, direba yaja shi zuwa sashin Hajiya......! Mommyn Twins ce Daddy na zaune a parlour'n Hajiya bayan sun gaisa, Hajiya tayi ta kawo masa hirarraki, yana amsata amma gaba d'aya hankalin sa na ga maganar da take cikin ransa, wanda yake tunanin tinkarar Hajiyar da shi. Daddy ya gyara zama ya fuskanci ta da kyau ya yi karfin halin soma magana. r"Hajiya dama wata magana nake tafe da shi, amma bansan da wace fuska zaki fiskanci lamarin ba, amma Hajiya dan Allah ina so ki fahimce ni, a matsayin ki na uwa a gare ni, nasan kinfi kowa son ganin farinciki na, yin tawassali da Allah babu abin da yafishi dad'i da samin nasara a rayuwa, ka yadda Allah shike da ikon yin komai a duniyar nan, duk abin da ya sami bawa da sanin ubangiji duk kuma abun da kaga ya faru da kai dama rubucacce ne cikin kaddarar ka sai dai wani yazamo sila, shirka haramun ce babu laifin da Allah baya yafewa bawa har idan yamutu yana aikatashi face shirka, haramun ne shaidar zur abin da baka da tabbaci akan sa ka tabbatar da cewa hakan ne." da sauri Hajiya ta ce "To Abubakar ni ban gane in da wanna batun naka ya dosa ba, wai wa'azi kake yi min ko me? tun kafin kazo duniya nake jin wa'azi, ai naga kamar shirin fita kayi katashi ka tafi Allah ya bada sa'a, wa'azi kam ai andad'e ana jin sa." Daddy ya d'an yi shiru da wasi-wasi tap cikin ransa ya gyara zama yana son dai-dai nutsuwar sa, kai tsaye yasoma fad'in "Hajiya ba haka ba, abin da nake tafe da shi nake son sanar miki shine, ina so na bawa Abdulrahim auren FEERYAL, saboda wasu dalilai idan da zaki fahimceni da zan zayyano miki dalilan nawa, kuma nasan zaki bani goyon baya..." wani irin zabura Hajiya tayi tamkar taga wani muhimmin mugun abin tsoratarwa. wani irin bugawa kirjin Ajmal daya sako kai zai shigo parlour'n ya yi har sai da ya kai hannu ya dafe kirjin nasa, dake bugu dum-dum-dum!. wani irin bakin abu yaga ya gilma masa a ido, ya juya da sauri ya koma side d'in su. a parlour'n kuwa Hajiya ta mike tsaye a zabure take fad'in "Abubakar kasan me kake fad'a kuwa! ko kunne na ne yajiyo min ba dai-dai ba? aljanar kake son aurawa abokin turawa! to bari kaji wlh ko bayan ba raina banyarda ka aura masa ita ba, bama shi ba ko wani d'a a gidan nan kai koma waye har idan da dangantaka sakani na da shi, wlh ban yarda ba ban yafe maka ba Abubakar idan ka aurawa wa wani jikana, wannan mayyar aljanar ruwan bare jikana na fari abokin turawa!." Daddy da yaji kamar ciwon sa zai tashi sabar tashin hankalin da ya shiga agurin, dama yasan da kamar wuya Hajiya ta yadda. ya dafe kirjinsa da ya soma yi masa zugi ya ce "Hajiya da zaki fahimce ni ki bani dama na kawo miki dalilai na." "Rufamin baki dalilan banza da lilan hofi, ai baka da wani dalilin da zaka gayamin akan auren mutum da aljana, ai in zaka mutu babu abin da zai sa ayi auren nan, ko mutuwa zakayi sai dai ka mutu Abubakar." Hajiya ta juya ta shige d'aki tana falle zane tana gyara d'aurawa sabar masifa. bata karasa ciki ba takuma juyowa ta dawo "Ni za'a kawowa zancen banza zancen iska, to maza-maza kaje ka fita da yarinyar nan a gidan nan yanzu, idan kuma ba haka ba ni nafita na bar maka gidan ka, baka zab'eta a kaina ba ai dama shi yasa ka masa kan ta zauna wai ana bincike, ai ita yakamata ayi bincike a kanta ba wasu ba, to wlh idan baka kori yarinyar nan ba saina sassab'a maka." Hajiya takama jan hanci tana cigaba da fad'in "Dama ashe abin da yasa kaki rabata da gidan nan ke nan, Abubakar nasake fad'a maka in zaka mutu abokin turawa bazai auri yarinyar nan ba, yaushene ma yayi aure da za'a sake masa wani auren, kai wlh ko shekara goma ya yi da yin auren fari idan wannan aljanar yarinyar ce bazaiyi na biyu da ita ba, tashi maza ka fita min anan ni zaka kawo wa tsiya." Daddy ya mike jiki ba kwari ya fita. A b'angare Ajmal kuwa d'akin sa ya shige ya kulle kansa ciki. ya kafa kansa jikin garu-bango yana jin wani irin azaba cikin ransa. yarika dukan jikin garu-bango yana fad'in "Why Why why! ya akayi nayi nauyin baki ne, ni nake son FEERYAL Daddy ba Ya Abdulrahim ba." ido ya rumtse da karfi tare da buga kanta a jikin bongo, sai kuma ya zame kasa ya zauna ya mike kafafunsa, ya jingina bayansa da jikin garu yana juya kai hannunsa na dafe da gefen zuciyar sa, ya yin da idanunsa ke a rumtse. Daddy kuwa yana fita ya shiga mota direba yakai shi office sai dai me yakasa zama office d'in ya fito yasa direba ya maida shi gida. Aunty ta mike tsaye da sauri ganin Daddy ya ya shigo bedroom d'in ta. ta ce "Daddy ba dai mantuwa kayi ba, naga ka dawo da wuri." zama ya yi yana cewa "Zauna Fad'imatu muyi magana." Aunty ta zauna tana kallon shi da alamun soma shiga fargaba. "Fad'imatu." Daddy ya kira sunanta. "Na'am Daddy." ta amsa zuciyar ta na d'an harbawa. "Jiya magabatan wannan yaro mai son Feeryal Major Sadam sunzo, nasa akayi musu masauki a masaukin ba'i na cikin company; sunzo nima masa auren ta sannan sun taho da shirin su sunaso a yanka musu sadaki, da sa rana duk a jiyan, dan suna tafe da kud'i idan aka yanka sadaki subiya nan take, a samusu ranar da bazai wuce wata guda ba. sai dai ni na ce musu nayi mata miji tuntuni, kuma a halin da ake ciki zan aurar da ita wa mijin da nayi mata nan da kwanaki kad'an, Fad'imatu na sami Hajiya da ma nasan ba lallai ne ta aminta da abun da naje mata da shi ba, ina da yakinin bani kad'ai ba kowa zai amfana da abinda nake son aiwatar wa." Aunty ta jinjina kai kamar ko da yaushe acikin yadda da maigidan nata take ta ce "Insha'allahu duk abin da kake son aiwatarwa alkhairi ne, amma mene ne shi d'in Daddy?." numfashi ya sauke sannan ya ce "Zan aurawa Abdulrahim Feeryal hakan ne kawai zai kaini ga tsira daga farmakin da ake kawo min cikin bacci, wanda bansan ta ina ne yake zuwa ba." zumbur Aunty ta mike tana girgiza kai da fad'in "Aa Daddy dan Allah kar ka soma, dan Allah kar kabar maganar nan ta fita na roke ka, kaje ka sami Hajiya ka ce mata dama fad'a kawai kayi ba zartarwa zakayi ba; Daddy ka rufa min asiri ya zanyi da rayuwa ta a cikin gidan nan idan wannan maganar ta fita, ya zanyi da Hajiya da Hajiya Halima da sauran 'yan gidan nan, Daddy so kake na tattara na tafi ko, dani da Feeryal d'in duka, dan Allah Daddy kar ka sake wannan maganar, Feeryal kam ma tana da wanda zata aura Major Sadam, ka bashi auren ta kawai." "Fad'imatu zauna dan Allah." Daddy ya fad'a yana ruko hannunta. kai ta girgiza ta ce "Aa Daddy tsoro nake ji dan Allah ka janye batun nan." "Ke ma ashe bazaki saurare ni kiji dalilai na ba, Fad'imatu kaf duniya babu wanda yake fahimtata sama da ke, kin fi kowa sanin damuwa na, zauna dan Allah." jiki a sanyaye ta koma in da ta tashi. ya dube ta da kyau kana ya soma magana "Na jima ina tunanin wanda zan zab'awa Feeryal a matsayin abokin rayuwarta, tun lokacin da ta fara tasowa, nake yi mata fatan nagartaccen miji, wanda zai kula da ita yaji kan lamuranta, a daren da aka rasa Feeryal ranar auren Abdulrahim, yasa kafa yafita nemo ta batare da wani ya sani ba, yaje ya kwato ta a hannun wad'an da suka so b'ata mata rayuwa, lokacin da ya dawowa da ita gidan nan tun a ranar naji shine ya dace da rayuwarta." zama Daddy ya gyara kana ya kira sunan ta "Fad'imatu kinsan wa yake citona cikin munanan mafarkan da nake, kuma me nake ji ake fad'a a kanta, Feeryal ce; cemin ake itace hasken kub'uta ta kar na barta tayi nesa daga rayuwa ta." a hankali yashiga bata labarin abubuwan da yake gani cikin mafarki wanda dama bai tab'a zama ya fad'a mata irin abubuwan da yake gani ba, sai dai idan ya farka ya ce mata, zasu kashe shi. sannan ya d'aura da fad'in "Dama ina da shirin aura mishi ita, tun a daren ranar auren shi naga dacewar hakan, dalilin da yasa na dad'a karfafawa kuwa a shine mafarki na, Fad'imatu shin kina so na dad'a kasancewa cikin yanayin da na shiga a kwanakin baya ne, ki karfafa min gwuiwa mana, ina ji a raina da gaske Feeryal alkhairi ce a rayuwar mu, zamanta a cikin mu alhaki ne." Aunty ta sauke numfashi ta ce "Daddy bana fatan ka sake kasancewa cikin halin da ka shiga a baya, amma Daddy Hajiya fa bazata tab'a amincewa ba, sannan ita kanta uwar Abdulrahim Hajiya Halima bazata amince ba, sannan shi kansa Abdulrahim d'in da 'yan'uwan ka da kowa da kowa ma, ba lallai ne su amin ta ba, me zai hana idan ta auri Major Sadam d'in ace ya zauna da ita a garin nan, ai kaga muna tare da ita ke nan bamuyi nesa da juna ba." Daddy ya ce "Amincewar Hajiya kad'ai nake bukata, bayan ita bana bukatar kowa sai ya aminta." Aunty tayi shiru tana tunanin taya hakan zata kasance, lallai kuwa matsala yanzu ne zata kunno kai. Da kyar Ajmal ya samu ya rarrashi zuciyarsa, yafito cikin 'yan'uwan sa. Hajiya abin bai mata ba da daddare tayi tattaki zuwa sashin Daddy, takuma jaddada masa ko bayan ranta akayi auren nan bata yafe ba. Hajiya bala'i take tana fad'in "Sabo da aljanar yarinyar nan ta gama shiga jikin ka, shine kake nima ka kakabawa abokin turawa ita dan shima ta shige jikin nasa ko, to kai da kayi gayyarta kaje can ka karata badai jikana ba, wlh takar baki idan ka kuskira sai ka biyani nono na! kuma gobe-goben nan nake son yarinyar nan tabar gidan nan, idan bata tafi gobe ba ni zan tafi kuma kar ka sake kaje in da nake bani ba kai ke nan." Hajiya ta juya ta fita tana cigaba da bala'i. Wad'annan kalaman da Hajiya ta fad'a sunyi mugun tsayawa Daddy a rai, dan kalmace mai girman gaske akan kowani d'a idan uwa ta gaya masa. kalaman sunyi masa girma har sai da yaji kamar ciwonsa na shirin tashi. ranar a daddafe ya kwana kirjinsa na zafi. washegari da safe Daddy ya kira Bappa Salihu na Yelwa mahaifin Mommy kanin mahaifin su, yasanar masa abun da ke faruwa. Bappa Salihu ya ce "Hajiya Hanne ke nan, wannan magana bazata yuwu a waya ba zanyi tattaki nazo Lagos d'in, insha'allahu gobe zuwa jibi zan shigo Jos nahayo jirgi na iso nan Lagos d'in." Daddy ya yi ta masa godiya kana ya katse kiran. lambar Abdulrahim ya kira ya ce yazo yana niman sa. batare da b'ata lokaci ba ya shigo parlour'n nasa. ya nimi guri ya zauna tare da gaida Daddy ya amsa yana kuma duban sa da kyau, sannan ya d'anyi gyaran murya kana ya ce "Abdulrahim nakiraka ne domin nagaya maka hukuncin dana zartar a kanka, duk da kakarka ta nuna rashin amincewar ta, bazanyi kasa a gwuiwa ba zan sanar maka kafin lokacin dana yanke yazo, Abdulrahim zan aura maka Feeryal bayan ganin dacewar hakan na zartar da hukuncin." da karfi ya yi wani irin d'agowa ya dubi Daddy. Daddy ya jijjiga kai tare da fad'in "Kwarai kuwa hukuncin dana yanke ke nan." kasa ya yi da kansa batare da ya ce ko mai ba. Daddy ya ce "Tashi kaje idan na tsaida rana zan sanar maka." da sauri ya ce "Amma Daddy." "Amma me Abdulrahim musu zakayi min?." kai yakuma sunkuyar wa, bai kuma magana ba, a sannu ya mike ya yi waje Daddy yabi bayan sa da kallo. Abdulrahim na fita Daddy ya kira Mommy a waya ya ce tazo yana son magana da ita. Mommy ta shigo ta same shi a parlour ta nimi guri ta zauna. Daddy ya dube ta kana ya ce "Hajiya Halima nakira ki ne domin na sanar miki abun da na yanke kan d'ana, bana so ace kinji maganar a gun wani, ki kalli hakan a kan rashin adalci; ina sanar miki hakan ne dalilin ke ma uwa ce a gare shi, kafin na zartar da hukunci yana da kyau na sanar miki, zan d'aurawa Abdulrahim aure da Feeryal, ni mahaifin Abdulrahim ita na zab'a masa a matsayin mata." Daddy na kaiwa nan ya mike yanufi kofar fita wani irin daramm damm Mommy taji tamkar saukar aradu aka, sabar tashin hankali da d'inbin mamaki da jin abun tamkar almara kasa iya furta komai tayi. tabi shi da kallo har ya b'acewa ganin ta. sai sannan ta sauke wani uban ajiyan zuciya kamar wacce ta suma ta farfad'o. ta ce "Tabd'ijan wlh karya ne bazai tab'a yuwuwa ba!." A haukace Mommy ta mike tabi bayan sa, ta hango har ya shiga mota direba ya ja shi sun nufi get. sashin Hajiya ta nufa tana zuba ruwan bala'i bata ko ganin gaban ta. tun daga bakin kofa take fad'in "Hajiya ciwon nan ya fara tab'awa Alhaji kwakwalwa fa, kinji me yake gaya min yanzu kuwa, wai zai aurawa Abdulrahim wannan aljanar yarinyar." Hajiya ta ce "Wato bai janye maganar ba ke nan, to ai sai ya yi mugani, ba sai ma ya ganta a gidan ba." ta fita fuuu Mommy tabi bayan ta. "Ina aljanar take fito kibar gidan nan, tun da bana uban ki bane." Hajiya ta fad'a sanda suke shiga parlour'n Aunty. Aunty ta mike tsaye da sauri. Mommy ta wurga mata kallon banza sannan ta ce "Kina tunanin yadda kika sami kan Alhaji haka zaki sami na d'ana, wlh karya kike ba dai d'ana ba kam." tuni Hajiya ta wuce d'akin Feeryal ta na fad'in "Ina kike fito kibar gidan nan jikana yafi karfin ki." Hajiya ta shiga raba ido cikin d'akin ganin bata ciki, ta wuce har cikin bayi, nan ma bata nan. ta fito tana fad'in "Ina kika b'oye ta fito da ita yau bazata kuma kwana gidan nan ba." Aunty bata ce kala ba suka karaci masifarsu suka gama bincikota basu ganta ba suka tafi. sai da suka tafi tukun Feeryal dake kichin suna aiki da Baba Rabi ta fito. dan tajiyo hayaniyar su kuma tasan a kanta ne bai wuce ace tabar musu gida ba, dan Aunty bata sanar mata da abun da ke faruwa ba. Mommy bil hakki ta d'aga bori babu wanda ya isa ya aurawa d'an ta Feeryal. a gefe guda ma Hajiya na nata, a d'aya gefen kuwa labari daya isarwa Umma Karima kaukane kawai batayi. Bappa Salihu baiyi kasa a gwuiwa ba ya diro Lagos bayan maganar su da Daddy da kwana biyu, ya iso da daddare. bai bari sai gari ya waye ba ya iso sashin Hajiya. Hajiya tayi mamakin ganin sa a irin wannan lokacin. Hajiya ta cewa Kulu ta kawo masa abinci Bappa Salihu ya ce "Bar abincin ki Hajiya Hanne bacin abincinki bane ya kawo ni." Hajiya ta d'aga hanci sama tana cewa "Yoo wata maganar aka gaya maka ke nan, nifa in akan batun auren abokin turawa ne da aljanar yarinyar nan ne, bafa zan zuba ido ina gani a kakabawa jikana damuwa ba." "Yanzu fisabilillahi Hajiya Hanne, ya kyautu ke nan kirika jifan d'anki da irin wad'an nan munanan kalamai, mutumin da ba wani cikakken lafiya yake da shi ba, kike son ki rika d'aga masa hankali, haba Hajiya Hanne har duniyar tayi miki dad'i irin haka, yau idan ya fad'i ya mutu wayake da asara, ni bazan yadda nasa iso akan wani dalilinki mara ma'ana ki salwantar min da rayuwar d'a ba, sabo da Yaya Shitu Fiya bashi da rai shike nan kike so ke ki baje kafa kizamo kece uwar kece uban, to kar ki manta muna nan mu rai uku masu rai, ba kuma zamu sa miki ido ki nima yiwa 'ya'yan mu baki akarin banza ba, musamman shi jigon mu Abubakar, wani irin shirme ne wannan, kiyi gaggawar janye furucinki a kanshi in ba so kike ki zamo ajalinsa ba, daga ya so had'a sunnar annabi shike nan kibi ki tada hankalin ki, bakin ciki kike da sunnar annabin?." Hajiya ta ce "Ni dama ai ban masa baki ba na gaya masa ne kawai bai isa ya aurawa jikana aljana ba." Bappa Salihu ya ce "To ai ba jikan ki bane ke kad'ai, kin san munfiki iko da Abubakar." Hajiya ta ce "To kuzo ku zauna da 'ya'yan ku ai dama tun ba yauba kuke nuna min bushashshen iko da gadara, nifa gara na koma gun dangina ma, dana zauna ana gwada min wani gadara, in dai aure ne da wannan aljanar ko bani gidan nan baza'ayi sa ba." Hajiya ta mike ta shige d'aki ta soma tattare-tattaren kaya, tana mita. Bappa Salihu ya mike ya fita yana girgiza kai da fad'in "Hajiya Hanne ikon Allah." Washegari da safe bayan sallar asuba Daddy ya shigo sashin Aunty, tana kan sallaya yazuba mata goro da minti a gaban ta. da sauri ta d'ago ta ce "Daddy wannan fa?." zama ya yi a bakin gado sannan ya ce "Na auren Abdulrahim da Feeryal ne da aka d'aura yanzu.......! *Masha'allah anan wannan littafi na biyu ya kawo karshe sai mun had'u a littafi na na uku*πŸ€— *FEERYAL littafin kud'i ne ki biya domin karantawa cikin aminci 500 account no 3170524141 Rashida Salihu first bank. ki tura shaidar biya ta Whatsapp number ta 08034690723 ina maraba da ku masoya na ni ma ina kaunar ku*πŸ€— Bari muzo mu raka FEERYAL d'akin ABDULRAHIM kowa ya tafi cikin shiri fa dan bamusan ya zamu tarar uwargida Kuraiba baπŸ˜‚πŸ€Έβ›ΉοΈ